Search
You have no alerts.

    Tsutsar Nama Book 3 part 3

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’‰š’“š’†š’†


    …….Tsaff sashen nasa yake an gyara komai tamkar koman bai faru ba. Yasan aikin Mama Balki ne wannan. Dan hatta bedsheet ɗin saman gadonsa da blanket an canja su da wani fari tass mai ʙyau da masifar laushi. Bathroom ya shiga, can ma ɗin dai an tsaftacesa. Sai kawai yayi wanka tare da ɗauro alwala ya fito. Sai da ya fara gabatar da shafa’i da wutri sannan ya kwanta dan barci sosai ke cin idanunsa ga ciwon kai da baya raba ɗayan biyu a dalilin zaman sashen Ummie da yayi ne. Dan lafiya lau suka shigo gidan sai gajiya dake damunsa. Yana kwanciya kuwa barci mai nauyi yayi awon gaba da shi…
             Da asuba makarar da yayi ce ya sashi yin salla a ɗakinsa ya sake kwanciya. Barci ne mai nauyi ya ɗaukesa har ya manta ma safiya ce ba dare ba. Duk da kuwa shi da wahala kaga yana barcin safe ko rana. To inama yaga wannan lokacin kullum abubuwa sun ma kansa yawa. Idan har kagansa yini guda a gida yana hutawa lallai ba lafiya ba. Ko kuma akwai wani ʙwaʙwʙwaran dalili. Dan ko nan ta samu ya gudo dan ya huta baka rabashi da laptop ko tab a hannu yana harkokinsa.
          Cikin barci sautin knocking ɗin ʙofa ya addabesa. Dole ya buɗe idanunsa yana mai karanto addu’a. Sai da yaja kusan mintuna uku kafin ya miʙe zaune cike da takaicin wanda ke damun nasa. Agogo ya kalla goma da wasu mintuna na safe. Yaɗan furzar da iska kaɗan tare da zuro clean ʙafafunsa ʙasa. Nan ɗin ma sai da yaja wasu sakanni sannan ya ɗauki remote ya danna ʙofar ta buɗe kanta. Paah ne ya shigo, dan haka ya zuba masa ido kawai yana kallonsa. Sai kuma ya motsa lips ɗinsa a hankali ya ce, ā€œGood morningā€.
            Amsa masa Paah ɗin yay da, ā€œMorning dear, ka tashi lafiya?ā€.
          ā€œAlhamdullahā€.
        ā€œTo masha ALLAH. Dama Baba ne yazo tun ɗazun, da yace kar a tashe ka harka tashi da kanka, sai kuma ga baʙi munyi da ga human right, wai sunzo ne akan case ɗin yarinyar nan. Bamu san wanene yaje ya sanar musu ba a gidan nan. Muhammad wai miya kaika aikata al’amarin nan? Bayan nasan wannan ba halinka bane ba. Baka aikata a waje ba sai a cikin gida, haba Muhammad da mahaifiyarka na cikin lafiyarta mi kake zatoā€.
              Komai Maash bai ce ba har Paah ya gama maganarsa. Cikin ɓacin rai ya juya ya fita yana mai bashi umarnin fitowa yanzun nan ana jiransa kada ya ɓata musu lokaci. Da kallo kawai ya bishi na tsawon mintuna har biyu, kafin ya furzar da nannauyar iska ya miʙe. Bathroom ya nufa, bai wuce mintuna biyar ba ya fito. Ba tare daya canja pyjamas ɗin jikinsa ba ya zura bedroom slippers ɗinsa masu taushi farare tas kamar pyjamas ɗin nasa ya fito. Baiyi zaton a falonsa suke ba. Dan haka yay ɗan turus yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. Gaba ɗaya manyan gidan ne sai baʙi fuska mata biyu da maza biyu. Ɗauke idanunsa yay cike da basarwa, a dakile ya furta, ā€œGood morningā€. Yana kaiwa cikin kujera da ke gefen Baba prof alamar shi aka barma wajen zaman dama. Duk da dai kowa ya samu nasa gurin kasancewar falon bawai kujeru bakwai bane ba kawai. Yanda ya tsuke bakinsa da ga gaisuwar farko kowa ya fahimci jam’i yayi. Kuma bazai sake wata ba. Harara Hajiya Mammah ta watsa masa. Hakama Hajiya ʙarama sai da ta ɗan cija lips. Maman Malika ce kawai tayi ɗan murmushi da faɗin, ā€œAwwab babu dai wata matsala ko?ā€.
           Kansa ya jinjina mata. Sai kuma a hankali ya ɗan motsa lips ɗinsa ya ce, ā€œAlhamdullah Mamyā€.
         Da fara’a itama ta ce, ā€œAlhamdullahi mun gode ALLAH. ALLAH kuma ya kiyaye gabaā€.
         Baba prof, Paah, Uncle Abdullahi suka amsa da amin. Duk da dai fuskokinsu babu walwala suma. Kallonsa Baba prof yayi kamar mai nazari, kafin ya masa nuni da baʙin fuskar yana faɗin, ā€œBaʙine daga human right. Wai sun zo ne akan case ɗin yarinya da akai raping anan gidan. Sunyi-sunyi da ita tun jiya wai ta faɗa musu amma taʙi. Shiyyasa suka zo domin ganawa da kai, suna son a basu izinin yin bincike akan case ɗinā€.
           Shiru babu alamar Maash zai amsa kamar ba da shi Baba prof ɗin ke magana. Dan tun kallo ɗaya da yayma mutanen bai sake ba. A yanzu ɗin ma da yaji bayanin komai daga baba prof ɗin bai kallesun ba bai kuma tanka ba sai da ya mula dan kansa. Zamansa ya gyara cike da ʙasaita a wulaʙance ya kallesu a karo na biyu. Cike da gizagonsa ya furta, ā€œKo zan iya sanin mai kai report ɗin?ā€.
            Kallon juna sukayi, sai kuma cikin ʙarfin hali namijin dake facing Maash ɗin ya furta, ā€œRanka ya daɗe wannan ai sirri ne bama buɗesa. Duk wanda ya kawo mana report akan wani case yana da cikakkiyar kariya a garemu tako wace fuska. Amma idan munyi kuskuren shigowa bada izini ba ayi mana afuwa. Muna akan aikinmu neā€.
            Kamar bazai tanka ba dan har sai da kowa ya zuba masa ido a falon, sai kuma ya yunʙura ya miʙe yana faɗin, ā€œOkay tunda har kuka fahimci hakan da kanku ina fatan zaku gane hanyar da kuka shigo. Dan bana buʙatar fitowa na sameku koda a gate ɗin gidan nan neā€. Daga haka yay wucewarsa cike da takunsa na izza.
           Duk binsa sukai da kallo, sai da Baba prof ya katse yanayin cikin wayancewa ya saki murmushi da faɗin, ā€œKufa yi haʙuri, shima tun jiya ransa a ɓace yake da faruwar al’amarin. Wani dalili ne ma daya ɗan gitta yasa bai ɗauki mataki ba. Amma na tabbatar tunda har kuka zo nan da kansa zai nemeku idan ya huce. Maybe shigowar karan tsaye da kukayi mana ne ya tunzurashi. Amma in har komai ya dai-daita ni da kaina zan nemo ku in sha ALLAHā€.
         Badan sun gamsu da bayanin Baba prof ɗin ba suka miʙe. Sai dai sun tabbatar da yanda suka karanci tsagwaron rashin mutunci a fuskar Maash ɗin to lallai idan har ya dawo ya same sun komai zai iya faruwa. Har gate Baba prof yay musu rakkiya yana ʙara basu haʙuri. Sai da ya ga fitar motarsu sannan ya dawo. Zama suka sake yi jugum-jugum amma babu alamar Maash zai sake fitowa. Hajiya Mammah ce ta katse zaman shirun nasu da faɗin bara ta sake kiran Maash ɗin. Amma sai Baba prof ya dakatar fa ita akan ta barsa yana son yanzu shi yaje asibiti yaga yarinyar kafin su san ta hanyar da zasu ɓullo ma al’amarin. Sam bata so haka ba, sai dai ganin sauran duk sun bada goyon baya yasa ta yin shiru….

           Maash kam daga falon hanyar da zata sadashi da sashen Ummie ya nufa. Ya samu sashen na sabon ʙamshi alamar an masa gyara. Sosai yayi mamakin waye kuma? Tunda yasan ita tana asibiti. Yana shiga yaci karo da mama Balki na shirin fitowa. Cikin kasa ɓoye mamakinsa ya ce, ā€œMama kece?ā€.
         Murmushi tayi cike da kulawa ta ce, ā€œEh Alhaji ʙarami. Ai mutuniyar taka ce tun asuba data farka take ta roʙona nazo na duba mata Ummie, tasan maybe bata ci abinci ba. Harda kukanta. Dan haka ina yin sallar asuba gari yay haske nai shirin tahowa sai kuma ga Hayatu ma yaje kai abinci shine na biyosa ya kawoni. Gata nan har ma taci abinci tasha magani barci ya ɗauke ta. Sauri nake kuma na koma can asibitin yanzu dan zata iya ʙin shiga ruwan zafin dana bar mata itamaā€.
                Idanunsa ya ɗan lumshe tare da buɗewa a lokaci ɗaya. Sai kuma a hankali da silent voice ɗin nan nasa ya furta, ā€œALLAH ya saka da alkairi Mamaā€.
        ā€œAmin Alhaji ʙarami ai yiwa kaine. Bismillah ka shiga, Bara naje Hayatu na jirana zai maida niā€.
         Shiga yay ita kuma ta fice. Ya jima a ɗakin yana kallon Ummie har sai da kansa ya fara juya masa sannan ya fito. Da gaske sauʙi ya fara samuwa. Dan inda dane a yanda ya shigo ɗin nan komai barcin da take yi saita tashi kansa. Amma kalla jiya yafi zaman awa biyu amma harya fita bata ko motsa ba sai shine da ciwon kai ya addaba. Sashensa ya koma batare daya bi takan su Paah dake a falo ba. Yay wankansa ya shirya tsaff da shi. Bayan ya gama fesa turarurtukansa masu ʙamshi da tsada kala kusan biyar, shiyyasa ba’a gane ainahin turaren da yake amfani da shi yay zaman saka takalmi. Wayarsa da akai kira ɗazun bai ɗauka ba ya duba. MD ɗin companyn sa ne na Kano. Kiransa yay back, dan yasan akan maganar Musaddiq ne. Cike da girmamawa baturen mutumin ya gaishesa da ga can. Kafin ya ɗora masa bayani akan komai na Musaddiq ɗin ya kammala. Zuwa next week zai biyo jirgi zuwa nan Lagos daga nan sai ya wuce. Kamar yanda ya saba amsa wayarsa bata wuce ɗaya biyu koda zakuyi maganar awa ne ya amsa masa da ā€œOkayā€ kawai ya yanke wayar. Daga haka ya ʙarasa shirinsa ya fito.
        Hayatu da Tj kawai ya samu a falon suna jiransa. Bai zauna ba da ga tsayen ya amsa gaisuwarsu yana mai ɗan kallon agogon hannunsa mai shegen tsada da ʙyau. Sai kuma a hankali ya furta, ā€œLet’s goā€. Duk miʙewa sukayi, yana gaba suna binsa a baya, sai ma Hayatu ne dake ɗan masa bayani daya shafesu dan akan kasuwanci ne har suka iso gaban motocin da aka gama shiryawa domin fitar tasa. A tare guards ɗinsa da sauran ma’aikatan gidan suka dinga kawo gaisuwa da jajanta abinda ya faru, tare da masa addu’ar kariya daga sharrin duk wani abun sharri. A karo na farko ya ɗan saki gajeren murmushi tare da haɗe hannuwansa a waje guda alamar ya gode. Kamar ko yaushe yana baya TJ na mazaunin driver Hayatu a gefensa. Sai motar guards ɗinsa guda biyu ata gaba da baya su suna tsakkiya.
         Sam yawo da guards ɗin nan ba sonshi yake ba. Sai dai baida wani zaɓin daya wuce hakan saboda yanayin ʙasar tamu balle shi mai yawan maʙiya da masoya. Yasha tsallake tarko da aka shirya halaka rayuwarsa. Ana kusan ʙarshe ne da har ya samu harbi gab da shirin buɗe Companynsa na kano har aka harbesa, ALLAH dai ya taʙaita wahala harbin ya samesa a gefen kafaɗarsa ta hagu, daga nan ne Hayatu ya dage akan fitarsu da Guards ɗin.
          Tsaiwar motocin ya sashi kauda tunanin ya ɗago, ganin asibiti ya sashi ɗan kallon Hayatu daya buɗe masa ʙofa. Murmushi Hayatun yayi yana duʙar da kai da sosa ʙeya. Komai baice masa ba face ɗan girgiza kansa kawai ya zuro ʙafafunsa ya fito. Ciki suka nufa batare da ya lura da motocin su Paah ba, amma shi Hayatu sarai ya gansu dan tsakanin isowar tasu da tasu ma Ę“an mintuna neā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    To Masha ALLAH. Barkan mu da dawowa, ku tayani addu’ar dagewa na gama book ɗin nan kafin sallašŸ˜€šŸ„°

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’‡š’š’–š’“


    ……A ɓangaren su Paah kuwa isowarsu kenan asibitin suma. Ba kuma su san da su Maash a bayansu ba. Kai tsaye suka nufi cikin ɗakin bisa rakkiyar Mama Balki da sukai kira a waya. A tsorace cikin damuwa ta musu jagora dan bata san dami suka zo ba. Sai dai babu yanda zatayi dole tabi umarninsu. Sauʙin ma taga akwai Baba prof a tare da su. Sun shigo Samraah na zaune a kan gadon jingine da filo tana shan tea ɗin da Mama Balki ta haɗa mata a hankali. Fes take dan har tayi wanka saboda gashin ruwan zafi da Mama Balki tai mata bisa umarnin likitan. A hankali ta ɗago ta kallesu.

            Sai da zucuyata ta motsa da ganin waɗanda banyi zato ba. Idanuna na maida na rissinar ina ʙoʙarin haɗiye mamakina da Ę“ar tsorata. Sai da suka gama zama a inda Mama Balki ta nuna musu sannan na gaishesu cikin muryata da sam bata fita saboda kukan da naci na kwana da yinin jiya. Wasu sun amsa wasu basu amsa ba. Ni kuma sai banji damuwar komai ba tunda nasan dama ba lallai duk su amsa ɗin ba. Kasa cigaba da shan tea ɗin nayi ban kuma ɗago na kalla kowa ba a cikinsu, suma kuma babu wanda ya sake yin magana. Dai-dai nan aka ɗan sake knocking ʙofar. Mama Balki ta zabura domin buɗewa. Jin yanda take jaddada kalmar sannunku da zuwa cikin jin daɗi ya sani ɗan ɗago idanuna na kalla ʙofar. Tamkar abin shiri sai karaf suka faɗa a cikin nasa. Wani irin ɗan jan nasan yayi yuuuu zai lumshe nai saurin fara ɗauke nawa da maida kaina na duʙar. Sai kuma naji duk zaman yama gundireni, ga wani bugawa da zuciyata keyi dan harga ALLAH ko ganinsa tsoronsa yake ʙara min, ni kaɗai nasan kalar masifar dana gani a daren shekaran jiya hannun mutumin nan, dan haka ko matsoraciya kika kirani a wannan gaɓar Bily ni bazan damu ba. Kofin tea ɗin na ajiye a side drawer ɗin gadon na zame a hankali na kwanta tare da lumshe idanuna. ʘasa-ʙasa na tsinkayi wata muryar dattijo da kamar na taɓa jinta na masa magana. Banji amsar daya bashi ba kasancewar shi dama idan zai yi magana sai in yaso kowa ya jisa ne. Ya ringa yinta acan ʙasan maʙoshi kamar mai jin haushin mutane. Kaɗan nai ʙoʙarin buɗe idanuna dan ina son ganin mai muryar nan sai naga ya nufo inda nake gadan-gadan. Sai da zuciyata ta sake harbawa. Babu shiri na maida idanun nawa na lumshe. A bazata, matuʙar bazata naji alamun rankwafowar mutum da mayataccen ʙamshin turarensa da saukar numfashinsa akan fuskata. Ai babu shiri na ware idanuna. Shi ɗin ne kuwa, gaba ɗayansa yamun rumfa hannayensa duka biyu ajiye a saman gadon ta gefe da gefena. (Kambu! Anya mutumin nan nada kunya?) Na faɗa a zuciyata ina waro gaba ɗaya idanuna waje. Amma shi sai ya wani kaɗa min cat ɗin nasa da ɗage gira hankali kwance. Tuni ʙwalla sun cika min ido, cikin marairaicewa na shiga motsa lips ɗina zanyi magana. Sai kawai naji saukar yatsarsa a saman bakin nawa, idanunsa cikin nawa, cikin salon lumshe idanu da maida muryarsa low sosai ya ce, ā€œShiii!! Bana son surutuā€.
         Kunya takaici suka lulluɓeni a lokaci ɗaya. Gefe na kauda kaina tare da ture yatsansa daga saman lips ɗina, dan kalmar baya son surutun faifan taswirar daren shekaran jiya ta dawo min da shi fes. Hannun ya saka ya taro fuskar tawa ya maidota inda take. Baki na tura masa, ina son na hararesa amma shakkarsa da kwarjininsa sunyi masifar min ɗaurin goro, ga mayataccen ʙamshinsa dake tsarga min zuciya.
            ā€œBakin nan yana buʙatar wani abu ne halan?ā€ ya faɗa cikin soft voice yana ʙoʙarin maida yatsarsa a saman lips ɗin nawa. Hannu na na kai da sauri na rufe bakin ina zaro idanu, amma shi ko gezau zama ka iya rantsewa ba shine ke maganar ba. Hankalina sake tashi yayi na saci kallon inda Ę“an gidansu suke. Duk suna nan a ɗakin har Mama Balki ma. Tamkar zan fasa ihu idanuna cike da ʙwalla na ce, ā€œDuk suna kallonmu faā€.
           ʘoʙarin juyawa yay zai kallesu, ai bamma san na kai hannuna ba da sauri kan fuskar tasa na dawo da shi.
       ā€œWhat? kuma. Bakin ce na faɗa musu ne su fita kina son mijinki ya ɗanyi kissing ɗinki baā€. Ya faɗa cikin salon kashe ido da ɗan ɗage gira sama murya can ʙasa kamar mai raɗa yana ɗora hannunsa kan nawa da nake ʙoʙarin janyewa daga fuskar sa.
               Harararsa na ɗan yi hawaye na cika min ido na ce, ā€œALLAH ya kiyaye ni yaushe na ce hakan? Kuma ni ba Ę“ar iska baceā€.
         ā€œOh reallyā€. Ya faɗa cikin ɗage gira sama yana ɗan taɓe baki kaɗan da sake matso da fuskarsa daf da tawan. Wani irin bugawa zuciyata ta shiga yi da sauri-sauri tamkar zata faso ʙirjina ta fito. A hankali na fara jin saukar iska da ʙamshin mouth freshener mai ʙamshin strawbarry. Luff nayi zuciyata na sauka a hankali daga bugawar da take da motse-motse a cikin ʙirjina, harda tura baki batare dana sani ba.
            Ɗal ya ɗalle lips ɗin da yatsunsa murya can ʙasa ya furta ā€œI’m not interested maida bakinā€.
        Cikin sauri na buɗe idanuna wani irin tuʙuʙi na turnuʙe min zuciya da takaicinsa. Dai-dai nan yake ɗagawa da ga duʙowan yana wani yin fuuuu da idanun nasa. Jinai kawai hawayen da nake riʙewa sun wani irin silalowa a hankali…

           Maash kam da ya ɗago kallo ɗaya yayma kowa na ɗakin ya ɗauke kansa tamkar baiga irin kallon da duk suke masa ba na tsantsar mamaki da tu’ajjibi. A zafafe Hajiya Mammah ta yunʙura zatayi magana Baba prof ya girgiza mata kai alamar kar tace komai ba. Badan taso ba tai shiru, sai dai kallo ɗaya zaka mata ka fahimci yanda ta gama cika tai famm. Duk abinda ke faruwa hankalinsa na kansu ta wutsiyar ido, amma yay tamkar hankalin nasa akan file ɗinta daya ɗauka yake dubawa. Dai-dai nan likitar da ke dubata ta shigo ɗakin Nurse biye da ita. Ita ta fara gaishesu, dan duk inda akaga Family ɗinsu ana gurmamasu saboda Maash ɗin.
           Sai da suka gama gaisawar sannan shi da bai ko kalleta ba ya ɗago shanyayun cat idanunsa ya ɗan kalleta, sai kuma ya kauda kansa cikin dakewar nan tasa ya mika mata takardar daya zare jiya a cikin file ɗin ya miʙa mata. Amsa tayi cikin mamaki, sai kuma ta kalla takardar. Ɗagowa tai cikin rashin damuwa, sai ma gani da take ai tayi abin arziʙi dan haka baki a washe ta ce, ā€œSir komai da ya kamata mun rubuta kamar yanda binciken mu ya bamu akan fyaɗen, dan a yanzu haka ma muna muku albishir ɗin samar da ʙwararriyar lawyer da zata tsaya mata akan case ɗin. Yau kuma zan kai report ɗin ma police dama izininku kawai nake jira kasancewar ita Hajiya tace ba huruminta bane sai kai yayanta kazo. Amma gaskiya sir ina ʙara bada shawaran kowa ya aikata irin wannan zalincin ga baiwar ALLAHr nan shima ya ɗanɗana kuɗarsa. Dan ALLAH ne kawai ya taʙaita al’amarin da zata ma iya kamuwa da matsalar yoyon fitsari. A yanzu haka ma dole tana buʙatar kulawa sosai saboda ɗinkin dake jikinta abin sam babu daɗi, dan ban taɓa ganin case ɗin fyaɗe na tsagwaron zalunci irin wannan ba. Banama jin mutum ɗaya ne ya aikata abi…..ā€
             ā€œIna buʙatar sallama by nowā€.
        Ya faɗa cikin katseta da yanayin da kowa ya kasa fassarawa daga garesa. Sororo likitar tayi tana kallonsa. Sai kuma ta ɗan marairaice fuska cikin nuna damuwa ta ce, ā€œSir ko akwai wani kuskure da mukayi ne anan ɗin? Wlhy duk kulawar da kake buʙata muna kan bata ita yanda ta kamata. Yanzu fa nake maka bayanin har lawyer ʙwararriya mun samar akan case ɗinā€.
            Komai baice ba, sai ma ɗauke kansa da yay cikin nuna ʙosawa da maganar tata. Da yaga bata da alamar fahimtar shirun yake buʙata sai kawai ya nufi gadon da Samraah take cikin takun ʙasaita da bajinta hannayensa duka zube a aljihu. Duk abinda ke faruwa ina jinsu, dan haka zuciyata ke wani irin gudu raina fal mamakinsa. Guy ɗin nan he is stubborn mutum wlhy. Rayuwarsa har mamaki take matuʙar bani, mutum kamar wani dutsi baka taɓa iya gane gabansa da bayansa. Cak ɗin da aka ɗagani ya dawo dani hayyacina, sosai na zazzaro idanuna waje cikin matuʙar mamaki da ruɗani, rawa lips ɗina suka kamayi. Da ʙyar na iya haɗa kalmar, ā€œMi…miye haka kake yi?ā€.
          Ko kallona bai yi ba, sai ma takawa daya fara a hankali babu wani alamar jin shi yayi ba dai-dai ba ya bi ta tsakkiyarsu ya fice. Nikam ai sai naji bazan iya jurewa ba kawai na cusa kaina cikin ʙirjinsa tare da saʙalo duka hannayena ta wuyansa na saki kukan da ban san dalilin yinsa ba……..āœļø

    Ehem ehem Yayanmu ikon ALLAH, na Samraah bada kanka a sare kace ma su baba prof ya faɗi🤣🤣🤣

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’‡š’Šš’—š’†

    …….Da sauri Hayatu dake tsaye daga bakin ʙofa yaja da baya kansa a ʙasa yana ʙoʙarin ʙumshe dariyar dake neman kufce masa. Isowarsa dai-dai saitinsa ya sashi haɗiye dariyar da ʙyar ya buɗe masa ʙofar da sauri yana ʙoʙarin matsawa.
         ā€œKuzo da kayanā€.
    Ya faɗa a hankali dai-dai yana ficewa gaba ɗaya daga ɗakin.
             ā€œA lallai Mu’azz ka haifoma kanka jaraba wlhy.ā€
        Hajiya Mammah ta faɗa cikin tafa hannaye da riʙe haɓa. Babu wanda ya iya cewa da ita komai dan duk abin faɗar ya gudu musu a bakuna. Sai ma Baba prof ne daya motsa a hankali kamar wanda ʙwai ya fashewa a ciki yabi bayansa. Dole duk suma sauran duk suka motsa suka take masa baya. Sai da suka gama fita Hayatu ya ʙarasa gaban doctor ɗin. Kallon Mama Balki yay yayi murmushi. Itama sai ta murmusa tare da nufar kayayyakin su kawai ta shiga haɗawa. Doctor data gama shiga cikin ɓacin rai kallon Hayatu tayi zatai magana. Da sauri ya katseta da faɗin, ā€œDoctor kiyi haʙuri kawai ki bada takardar sallamar nan. Dan wlhy boss da kike gani baya magana biyu. Tunda ya yanke hukunci ya yanku, ya kuma fiki sanin muhimmancin wannan patient ɗin takiā€.
          Cikin ɗan ɓacin rai ta ce, ā€œWane muhimmancin ta ya sani anan?. Ana gaya masa haɗarin da yarinya ke a ciki saboda zaluncin da akai mata yana nuna kamar ma baya fahimta. Ni ban taɓa sanin guy ɗin nan stubborn bane sai yau. Idan ma ɗakin ne bai masa ba way not yay magana sai a canja mata da waniā€.
        Murmushi kawai Hayatu yayi dan ya fahimci bafa zata fahimta ba. Itama sai ta fita rai a ɓace tana mita dan gani gake shima Hayatun neman raina mata hankali yake yi. Binta kuwa yayi bayan ya amshi kayan da Mama Balki ta haɗa suka fito tare. Yana zuwa office ɗin doctor ta miʙo masa takardar sallamar a harzuʙe. Komai baice mata ba ya ɗauka ya juya abinsa ya fito.
              Samunsu yay suna shiga mota, dan shi gogan nasa ma har ya shige abinsa. Gaba ya buɗe ma mama Balki ta gefen sa ta zauna, shima yana ʙoʙarin shiga Baba prof ya ʙaraso wajen, umarni ya bama Mama Bilki kan ta fito ta koma motarsa, shi kuma ya shiga gaban ya zauna yana bama Hayatu umarnin suje KARAMCI HOSPITAL asibitin Hajiya ʙarama kenan. Amsawa Hayatu yay yana satar kallon Maash dake a baya tare da Samraah ta cikin mirror. Jingine kansa yake da kujera idanunsa a lumshe tamkar bai san mike faruwa ba. Shi kuma ya tabbatar duk yana jinsu. Kallo ɗaya yay ma Samraah dake kwance kanta a saman cinyar Maash ɗin itama idanunta a rufe ya ɗauke kansa yana ɗan sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya……

            šŸŒæā¤ļøā€šŸ”„šŸŒæā¤ļøā€šŸ”„šŸŒæ

         Hajiya Sakeena na kai ʙarshen bayaninta Mansoor ya fasa wata gigitacciyar ʙara da ɗaga Centre table ɗin gabansu ya wancakalar. Babu wanda bai firgita ba. ʘafa yasa ya bugi table ɗin da masifar ʙarfi, badan takalmin dake a ʙafarsa ba babu abinda zai hanashi jin ciwo. Da sauri Attahir ya miʙe yana ʙoʙarin riʙo hannunsa da kiran sunansa. Amma sai shima yay wani irin wancakalar da shi gefe har sai da Attahir ɗin ya zube a kujera. Cikin zafin zuciya da basu taɓa sanin yana da ita ba ya nuna Hajiya Sakeena da Mamynsa da take wani irin kuka tamkar ranta zai fita. Cikin kaushin murya da rufewar idon da fushi ya haifar masa ya ce, ā€œNa tsane ku. Ku biyun nan ba bana son sake ganinku a rayuwata har abada. Kuma yanda kuka zama sanadin rabani da ita kuma na barku har abada!!!!!!ā€.
         Daga haka ya figi bag ɗinsa fuuuu zai fice. ʘoʙarin miʙewa Attahir yay cikin ʙarfin hali yana kiran sunansa. Yayinda Mamy tai wani irin fashewa da kuka ta bisa da gudu ta riʙo rigarsa. Ko juyowa ma baiyi ba yasa hannu ya kaɓe natan tare da hankiɗata yay ficewarsa. Kafin ta miʙe tabi bayansa tuni yama fice a gidan ko mai kama da shi babu a compaund. Nan ɗin ma fita Attahir yay a guje, sai dai yana fitowa napep ɗin data ɗauki Mansoor na barin ʙofar gidan. Komawa yay cikin gida da gudu bawan ALLAH duk ya ruɗe. Dan key ɗin mota yake lalube amma ya gagara ganin ko guda ɗaya. Haka ya sake fitowa da gudu ya fita shima ya tare napep ya shiga suka bi bayan Mansoor. Amma ko mai kama da shi basu gani ba. Har airport yasa suka bishi a tunaninsa can zaiyi. Sai dai nan ɗin ma babu alamar Mansoor ɗin. Abinda bai sani ba kuma Mansoor bai je airport ba, dan ya fahimci abu na farko da zasu farayi kenan dan haka yaje ya kama hotel anan anguwarsu da yasan bazasu taɓa tunanin zai tsaya anan ba. Na kwana ɗaya ya kama, dan daga yau zuwa gobe yake son sake barin ʙasar nan. Sam bazai iya zama ba. Gara yayi nesa nesa can inda bazai sake ganin kowa ba a cikinsu har ʙarshen rayuwarsa…

          Duk wannan budiri da ake Dad bai ko motsa ba. Yana zaune ne kawai kamar saʙago a falon. Ba haka Hajiya Sakeena taso ba. Taso ace tana gama bada labarin nan yanda Mansoor ya fusata shima Dad ya fusata ya dinga ɗirkar Mamy da jera mata kalmomin saki uku sannan yace ta bar masa gida. Amma ba komai, ko yanzu ma ai tasan ʙurar bawai ta ʙare bane ba. Dan ita shaidace akan zuciyar Dad tamkar akku kuturu yake. Kusan zuciyar tasa ce ma yau Mansoor ya kwatanta. Shi kansa shirun da yayi ta tabbatar zuciyar ce ta kume Ę“an maza wayaga kutu-ban-ban. Haka ta fito babu tausayi babu imani ta tsallake Mom da nunfashi ke neman ʙwacewa tai ficewarta. Acewarta ai itama haka Mansoor ya tsallake tata ɗiyar ɗaya kwallin kwal a duniya ya tafi babu tausayi balle imani bayan ya gama zana mata kalaman saki uku da gasa mata magana iya son ransa…

         Duk neman daya dace Attahir yayi ma Mansoor amma bai gansa ba. Dole ya haʙura cikin maɗaukakin tashin hankali ya koma gida ransa duk a dagule. Yana zuwa kuma ya iske Mamy a sume a farkon shiga falo. Tashi hankalinsa ya sake yi, dan ga Dad zaune tamkar saʙagon gunki zuciya ya kumesa tamkar shima ɗin ya suma. Baima san ya sunkuci Mamy yay waje ba cikin tashin hankali yana kwala kiran sunan drivernsu…..

        🪓🪓🪓🪓🪓

            
         KARAMCI HOSPITAL asibiti ne da zamu iya kiransa tsaka tsaki a girma. Dan bai kasance ʙaton gaske ba, bai kuma kasance ʙarami ba. A ɓangaren kayan aiki komai an wadatashi da shi. Duk da sunansa asibitin kuɗi ana aiki a cikinsa tamkar ʙyauta ne saboda sauʙi da sauʙaʙama al’umma. Hakan yasa mafi yawan talakawa suke saurin garzayowa jiyya da karɓar magani a cikinsa. Sai dai da yake komai nasu a tsare yake bazaka taɓa samunsa barkatai ba komansu a tsare yake.
          Kamar dai yanzu daya kasance rana ta fara ɗagawa, tako ina tsaftace yake sai ma’aikata dake ɗan kai kawo. Sannan shiru yake babu wata hayaniya ko yawan kai-kawon mutane bayan ma’aikatan saboda dokarsu ce irin yanzu ba’a zuwa duba mara lafiya sai yamma daga huɗu zuwa shida. Koda motocin su Maash suka iso ma da farko securitys ɗin ʙin tashi sukayi su buɗe saboda dokarsu ce ba’a ganin mara lafiya da dare ko safiya zuwa kafin cikar huɗu ko kai wanene, sai da Hayatu yay kiran number Hajiya ʙarama sannan securitys ɗin suka tashi cikin rawar jiki suka wangale gate ɗin. Suna gama parking Tsaki Hajiya Mammah tayi tana mita harda zagin Hajiya ʘarama lokacin da take fitowa. Babu dai wanda yace da ita komai.
            Hajiya ʙarama da kanta ta fito tana musu barka da zuwa dan ita tunda safe tana anan asibiti batama san sunje duba Samraah ɗin ba, ana gama case ɗin human right ta baro gidan. Cikin girmamawa ta gaida Baba prof.. ya amsa mata tare da mata bayanin maido Samraah da sukai nan dan a cigaba da kulawa da ita duk da dai shi ba sunanta ya ambata ba ya dai ce yarinyar dake jiyya. Amma kuma yanata tunanin a ina yasan fuskar yarinyar ne tun ɗazun. Cike da girmamawa Hajiya ʙarama ta amsa musu. Tare da musu jagora har cikin manyan ɗakunan jiyyarsu na vip na ʙarshe a daraja. Kowa baiyi mamakin rashin biyosu da Maash yayi ba, dan sai da Baba prof ya koma da kansa ya masa umarnin bari a shiga da ita kasancewar tare ya tafi da nurses dake ɗauke da gadon ɗaukar mara lafiya. Amma mi, ammakinsu ma ko kallon inda Nurses ɗin suke baiyi ba yanzun ma ya sake ɗaukarta camak yay cikin asibitin. Da kallo kawai Baba prof ya bisa abubuwa da yawan gaske na masa kai-kawo. Dan a wannan gaɓar ya gama sarewa da al’amarin jikan nasa. Sai ma yake wasiwasi anya kuwa shine ya aikata fyaɗen nan kamar yanda Nafisa ta faɗa. Dan al’amarin akwai matuʙar ban al’ajabi a cikinsa da ma ban tsoro.
          Acan daga ciki suma kansu kallonsa kawai suke kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa musamman ma Hajiya ʙarama da bata ga abubuwan daya faru a farko ba sai wannan ɗin. Dan baki ta hangame har sai da taji iska na kai mata har maʙoshi sannan ta iya haɗiyewa da ʙyarā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’”š’Šš’™

    ……Baba prof da bai koma ciki ba Nurse ɗin nan ya aika yace a sanarma su Paah su fito yana jiransu. Babu jimawa kuwa sai gasu ɗaya bayan ɗaya. Hajiya Mammah da Mama Balki da Hayatu sai shi uban gayyar kawai aka bari. Dan haka Baba prof ya sake aika Uncle Abdullahi yace yay kiran Hajiya Mammah saboda sanin halinta shi kuma baya buʙatar jan wannan maganar a waje shiyyasa ma da Maash ɗin yace a bama yarinyar sallama bai tanka ba. Ya kumace a kawota nan ɗin ne tai jiyya dan yasan asirinsu zai kasance a rufe tunda dai Hajiya ʘarama ta gida ce. Rai a ɓace Hajiya Mammah ta fito. Dan itafa gaba ɗaya an ɓata mata shirinta. Dan har magana ta gama da waccan likitar akan ta riʙe Samraah har sai nan da wasu Ę“an kwanaki da za’a iya fahimtar da ciki ko babu. Idan akwai ta fallasa a gaban kowa, idan kuma babu zata biya ko nawa ne aima Samraah dashensa sai kowa ya gama sani sannan ta tafi plan na gaba da za’a zubar da cikin wajen zubarwar a kashe Samraah. Sai kuma gashi cikin abinda bai wuce awa guda ba shegen yaron nan daya zame mata masifa da bala’i ya hanama rayuwarta rawar gaban hantsi tun yana mitsitsinsa ya rushe komai. Suma waɗan nan Ę“an human right ɗin sai taci abu takazansu dan sun mata aiki ba’a yanda tace musu ba. Idan kuma basuyi himmar ʙarasawa ba ALLAH sai sun biyata maʙudan kuɗinta…

         A ɓangaren Maash kuwa bai bar asibitin ba sai da aka gama yima Samraah dukan abinda ya dace. Duba magungunanta da sake bincikata in and out. Sai dai kuma anan ɗin ma dai doctor ɗin data duba Samraah ɗin dan ba Hajiya ʙarama bace saboda ba faninta bane. Abinda ta fara bincike da tambaya shine reping ɗinta akayi ne?. Shiru Maash bai tanka ba, bai kuma da alamar tankawar. Dan haka Mama Balki ta girgiza mata kai alamar a’a.  Rasa abin cewa tayi, dan dukkan alamu na jikin Samraah ya tabbatar da anje mata babu tausayi. Amma tunda ita Mama Balki tace ba haka bane sai ta tambayi mijinta, acewarta tana son ganinsa taji dalilinsa na nuna irin wannan rashin tausayi akan yarinya ʙarama. Kasa sake cewa komai Mama Balki tayi, sai ɗan satar kallon Maash ɗin da take ta gefen ido. Shi kuma yay masifar haɗe girar sama data ʙasa dan haka doctor ta haɗiye maganganunta a cikin rai dole.
           Ruwa tasa aka sakama Samraah dan tana buʙatarsa. Kasancewar akwai cannula ɗin wancan asibitin da ba’a cire ba sai hakan ya sauʙaʙa musu. Cikin ʙanʙanin lokaci kuwa barcin ya fara ɗaukarta dan shi dama suke buʙata tayin. Kiran wayar da Paah ya addabesa da shi ya sashi miʙewa cikin ɗan ɓacin rai sai dai bai ce komai ba bai kuma ɗaga wayar ba. ʘofa ya nufa abinsa batare da yayima ko Mama Balki sallama ba.

         Dishi-dishi nake ɗan hangosa, cikin mayen barcin dake ɗaukata a hankali batare da tunanin zai ma jini ba na furta, ā€œDan ALLAH ka dinga duba min Ummie akai-akai da bata abinci da maganinta. Kace kuma ina gaishet….ā€

       Cak ya tsaya daga yunʙurin fitar da yake yi, hannayensa duka a cikin aljihun wandon suit ɗin nasa. Tamkar mai ciwon wuya ya juyo da kansa a hankali ya zuba su a kanta. Idanunta masu cikar gashi dake a ɗan kumbure har yanzu a lumshe suke. Kallon kusan minti ɗaya yay mata ciff kafin ya motsa a hankali cikin tafiyar nan tasa tamkar baya so ya fice. Da kallo Mama Balki ta bisa, sai kuma ta saki murmushin da har haʙoranta suka bayyana. A hankali ta furta, ā€œHumm Alhaji ʘaramiā€. Sai kuma ta juya ta zubama Samraah da har ta fara sauke munshari idanun nata. Shigowar Hayatu ne ya katseta. Sallama yay mata dan yasan ba lallai yau ya samu damar sake shigowa asibitin ba tunda suna tare da boss. Gashi ma acan office jiransu ake sakamakon meeting da yasa Juliet ta tara na gaba ɗaya exco ɗin companynsa na cikin Lagos dama wajen Lagos masu alaʙa da abinda ya faru. Ya kuma tabbatar dole meeting ɗin zai jasu lokaci mai tsayi….
       
            🌺🌺🌺🌺🌺

         ā€œMagana ta gaskiya sai kun kula Attahir. Kun fa san Hajiya nada hawan jini. Yanzu badan ALLAH ya taʙaita ba a wannan faɗuwar da tayi fa komai zai iya faruwa. Dan ɗayan biyu ne. Paralysis ko heart attack. Saboda a kwanakin nan bincikenmu ya nuna zuciyarta na samun matsi sosai da yawan damuwa. Dan haka dan ALLAH ku kula. Zamu riʙeta anan zuwa 2days, ga wannan sai kaje konan pharmacy na asibiti ka samo dan data farka za’a buʙacesuā€.
         Numfashi mai nauyi Attahir ya sauke tare da jinjina kansa. Kafin a hankali ya ɗaura da yima doctor ɗin godiya sannan ya miʙe. Tafiya kawai yake amma shi baima san a inda yake jefa ʙafa ba. Dan shi a karan kansa yana buʙatar gadon ne a wannan gaɓar. Da ʙyar ya iya kai kansa pharmacy ɗin cikin asibitin ya miʙa musu takardar da doctor ɗin ya bashi kawai. Koda pharmacist ɗin ya duba ya sanar masa kuɗin baima bi takansa ba ya zaro ATM ɗin sa a wallet kawai ya miʙa masa. Hakama da aka saka adadin kuɗin bai wani dubaba ya amsa ya saka pin ɗinsa. Ledar ya amsa ya koma ɗakin da aka kwantar da Mamy.

        Har dare yay nisa babu Dad babu Mansoor. Babu kuma wanda ya kirashi koda sau ɗaya yaji yaya Mamyn take. Haka ya kwana cikin asibitin shi kaɗai, sai a washe gari bayan sallar asuba yana fitowa a massalaci fita yay a asibitin dan likita ya tabbatar masa Mamy zata iya kai sha ɗaya ma bata farka ba. Kai tsaye gidan ʙaninsa na ɓangaren Ummie ya nufa. Kakarsu mace ta rasu, sai tsoho mai ran ʙarfe da ya ragema Ummie kawai. Bai tsaya kwana-kwana ba ya zayyane masa komai dake faruwa. Sosai hankalin kakan nasa ya tashi, Attahiru na gabansa ya shiga bugama sauran Ę“aĘ“ansa waya duk yace suzo yana buʙatar ganinsu. Cikin ʙanʙanin lokaci kuwa duk sai gasu, ALLAH ya taimaka ma abin ya haɗa da weekend. Sake saka Attahir yay ya maimaita duk abinda ya faɗa masa. Suma ransu yay matuʙar ɓaci da wannan hali na Ę“ar uwarsu. Tun tana budurwa sunyi matuʙar yaʙi na ganin ta ajiye waɗan nan banzan halayen amma a banza. Kullum shari’arta da miji bata wuce akan wannan halin na son kuɗi da ʙarya. Gashi nan dai sai da takai ta watsa farin cikin gidanta da kai wa matsayar da suka dinga guje mata sannan hankalinta ya kwanta. Itama autar tasu Sakeena zama da gurɓataccen miji ashe ya canja musu ita ta koma irinta. Ɗunguma sukai su duka harda tsoho zuwa asibiti suka dubata. Sunko samu ta farka, haka duk suka jajanta mata sama-sama. Gaba ɗaya kunya ta hanata iya kallon kowa a cikinsu musamman ma Attahiru. Nauyin yaron take ji, dan yanada matuʙar haʙuri da kawaici. Duk irin banbancin da take nunawa tsakaninsa da ɗan uwansa bai taɓa ɗauka ya sakama ransa balle har taga ɓacin ran hakan akan koda fuskarsa ce. Yau ga wanda take matuʙar nunama soyayyar ya tsallaketa ya wuce akan mace. Duk da dai tasan ita duk ta jawo komai, sosai take jin dana sani da nadamar ʙwaɗayayyar rayuwarta a yau.

         Kwananta biyu a asibiti babu ko ʙyallin Dad. Tana son ta tambayi Attahir tana jin tsoron jin abinda bashi zuciyarta take son ji ɗin ba. Dan tana matuʙar so da ʙaunar mijinta. Hasalima kamanninsa da Mansoor ya ɗebo yasa take fifita soyayyarsa akan sauran yaranta. A ranar aka basu sallama. Tun da suka baro asibiti taga an ɗauki hanyar gidan babanta gabanta ke faman faɗuwa. Sai dai tsoro ya hanata tambaya har suka iso. Isowarsu babu jimawa suma su Amal suka iso. Dama suna Abuja gidan kawunsu ne. Sanda zasu wuce India su aka turasu can sai yau suke dawowa.
         Anan ɗin ma babu wanda yace mata komai har tsawon kwan biyu, abu ya dameta amma itama tsoron jin abinda bashi take son ji ba ya hanata iya tambaya. Zuwan Sakina biyu gidan babu mai tankama wani ita da ita. Su duka sun ɗauki zafi da juna tamkar ba Ę“an uwa ba jini ɗaya. Hasalima a baya sun fi shiri da juna matuʙa, dan rayuwar Ę“ammatanci gaba ɗaya Sakeenar a gidanta tayita ma..
          Attahir dai yakan zo da safe kullum kafin ya wuce aiki ya gaisheta. Hakama idan ya tashi sai yazo nan ya gaisheta sannan yake wuce gida. Kamar wasa a haka kwanaki suka dinga tafiya tana a gidansu. Ga baba ma sama-sama yake amsa mata gaisuwa. Baya shiga sabgarta baya kuma bata damar shiga tashi har gata da watanni biyu cif a gida. Su Amal ma tuni suka tattara kayansu suka gudu gida. Dan sunce bazasu iya zama gidan Baba ba saboda gidansu komai najin daɗin rayuwa suna da shi. Nan ko duk da Ę“aĘ“an baban maza sun tsaya akan al’amuransa shima kasancewar matarsa ba itace kakarsu ba abubuwa da yawa sai a hankali kawai. Ta kankane komai daga ita sai nata jikokin Mamy ma sai tayi da gaske wataran take samun abinci a gidan. Dan ma Attahir baya gajiya da kawo mata kayan shayi da Ę“an kayan maʙulashe. Amma itama da tuni yunwa ta kai rayuwarta ʙasa kamā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’”š’†š’—š’†š’

    ……..Tun fitarsu a ɗakin jiyyar yarinyar har barinsu asibitin akan idanunta ne. Numfashi ta sauke mai nauyi tare da ture ɗan kwalin kanta baya. Dauriya kawai take da danne abinda ke matuʙar cimata zuciya. Wayarta ta ɗauka a ɗan zafafe, tai Ę“an danne-danne tare da kaiwa kunnenta. Ana ɗagawa daga can ta ɗan sauke ajiyar zuciya. Sai kuma cikin ɗan farin ciki mai gauraye da sauran damuwa ta furta, ā€œSabon labariā€.
         Cike da zumuɗi daga can akace mata ā€œName fa Hajjaju masu Lagos da kayan cikinta.ā€
             ā€œHummm Jannifer bar batun wasa Please. Yarinyar nan ce fa suka maido asibitin nan yanzuā€.
         ā€œWhat! Kina nufin Samraah?ā€.
      ā€œYess. Yanzu haka tana nan tare damu. Ban san miya faru ba suka maidota nan ɗin. Naga dai mutuniyarki a zafafe cikin matuʙar damuwa kuma. Yanzu kam na fara zargin akwai abinda take ʙullawa. Na kuma yi alkawarin sai na bincikosa a koma ina taje ta bizne shiā€.
           ā€œKarki wani damu Hajjaju wannan duk mai sauʙi ne. Ko ni nan na isheta. Har mi akai akayi Alaja Nafee kuma. Matar da bata iya komai ba sai da shawaran banzan Madan Rubayya ɗin nan. Ni dai kawai yanzu shawaran da zan baki kawai kiyi ʙoʙarin ki kula da yarinyar nan da ʙyau, tunda dama tun farko kayanki ce. Kin zauna sakaci ne Alaja Nafee ta nema ʙwacewa. Banzama irinta da ta ʙare a ʙarʙashin guzumomi irin su Rubayya. Dan bana raba ɗayan biyu shakkar Rubayya ɗinne ya hanata taya yarinyar kafin ke, tunda itama ai mayyar ce. Saboda haka kiyi amfani da wannan damar akan ita yarinyar kiyita banka mata maganin da zai fidda mata sha’awar namiji gaba ɗaya a ranta, ina tabbatar miki da kanta zata kawo miki kanta tana kukan ki mora albarkacin jikinta. Haba Alaja Lawusa kamar baku bane Lagos ɗin. Ni fatana ma idan zakije honeymoon da ita aje dani koda a Ę“ar riʙon handbag ceā€.
         Dariya mai ʙayatarwa Hajiya ʙarama ta saki, tare da sake lume kanta a cikin kujera idanunta a lumshe tana siffanta cikakkiyar surar Samraah data jima tana birkita mata lissafinta. Dan tun randa Jannifer tayi kiranta ta sanar mata da zuwan yarinyar gidan matsayin gift da Mashi’a tai shirin kawoma Hajiya Babba dan ta kula da ita ta gama jin ʙaguwa da son ganin yarinyar. Saboda haka ta azalzali Paah suka dawo Nigeria washe gari badan ma sun kammala abinda ya kaisu ba. Koda suka iso tai ido biyu da Samraah sai da numfashina ya nema shiɗewa. Dan yarinyar irinsu ne ake kira da full option. Komai yaji yanda ya kamata. Sai dai kash abubuwa da dama sukai mata katanga da hakan, tayi ʙoʙarin riʙe kanta har zuwa sanda ta gama shiryawa sai kuma ga wannan abin ya faru da yay matuʙar ʙona mata rai, dan a yanzu haka ita kaɗai tasan irin kalar zafin yaron nan Awwab da take ji a rayuwarta. Wani irin kishi take ji tamkar ta kashe banza a wuce wajen dan son Samraah take na gaske. Har ma ta gama yankema kanta shawarar auran yarinyar zatayi ta ɗauketa daga Nigeria zuwa duk ʙasar da take so sai ta dinga kai mata ziyara….
           ā€œAlaja!ā€.
       Jannifer ta katse mata tunani. Firgigit ta dawo hayyacinta tana mai sauke nannauyan numfashi. Cike da basarwa taja ɗan sirrin tsaki da faɗin, ā€œSorry Jannifer na tafi wata sabgar ne kuma.ā€
         Dariya Jannifer ta ʙyalʙyale da shi daga can, cike da shaʙiyanci ta ce ko dai kin tafi tunanin kayan alatu baā€.
        Murmushi Hajiya ʘarama tayi tana mai cije lips ɗinta. Kafin a hankali ta ce, ā€œKe dai Jannifer sheɗaniya ce wlhy. Lallai da ace bakiyi ridda daga musulimci zuwa kiristanci ba da ba ʙaramar sheɗaniyar matar hausawa musulma akayi ba. Amma yanzu mun bar musu, dan inba ma wanda ya sani ba taya zai taɓa yarda kin haɗa iri da fulani. Humm ALLAH dai ya jiʙan General. Ya tafi yabar baya da ʙura. Maybe da za’a shawarcesa a dawo da shi duniya yaga Munirra ɗinsa yanda ta koma kamar bata taɓa haɗa jini da yan arewa da musulunci ba da dakansa zai kashe kansa ma wlhyā€.
            ā€œHummm Hajjaju kenan masu Lagos da jama’ar cikinsa. Ai duk nawa wasan yara ne. Idan kuna guri mu kuma wake ta tamu ʙananun ʙwari. Mufa a riddar kawai muka tsaya sai ɗan cinikin goron nan da muke kafawa a faifai da ɗan hutawar nan muna more ʙuruciya. Ku kuwa fa, idan akace ai tone-tone ai kema musulman sai sun gwammace riddar kikayi wlhyā€.
          ā€œUhhm to ya isa. Dan ke baki gajiya da zakuɗe-zakuɗe. Yanzu dai sai anjima idan na tashi zan zo gida na sameki mu ʙarasa. Dan zan ɗan shiga theaterā€.
         ā€œHummmā€ kawai Jannifer tace daga can tare da yanke wayar tana dariya. Itama sai Hajiya ʙaramar tai dariyar kawai tana ʙoʙarin ajiye wayar, a dai-dai nan wani kiran ya sake shigo mata. Ido ta zubama number na tsawon lokaci, YALLAʁAI ɓaro-ɓaro ya fito. Mamaki ya sake kamata dan rabon da mai number yay kiranta ta jima sosai, dukan tara-tara ʙirjinta ya shiga hi har sai da wayar ta kusa yankewa ta dawo a hayyacinta. Da sauri ta ɗauka tana miʙewa ta nufi ʙofar office ɗin ta murza key cike da rashin gaskiya….

          šŸ¤”Hummm wai ina matan nan suka dosa ne?  Sannan waye yay kiran Hajiya ʘarama kuma? Idan na fahimta dai Hajiya ʘarama na waya da Madam ne a farko, matar data ɗakko Samraah daga Abuja zuwa Lagos. Tab ɗin babbar magana. Ashe ita ɗin musulma ce shine tai ridda. Innalillahi wa-inna ilaihiraji’un. Anya wannan duniya kuwa. ALLAH mun tuba badan halinmu bašŸ˜­šŸ™.

          __

       THREE DAYS LATER

              Kwanaki uku kenan da faruwar komai. Sam Maash yaʙi yarda ya zauna da family ɗin nasa akan batun Samraah. Dan haka ran kowa a matuʙar ɓace yake. Amma shi ko’a jikinsa sai manna musu hauka kawai yake. Dan gaba ɗaya ma ya maida hankalinsa ne akan binciken yanda akai containers ɗin companyn sa suka ɗiba yara da wiwi saɓanin lodin kayan abinci. Dan suna shirin tunkarar Mr Paul ne da ʙarfinsu a court saboda sun shigar da ʙara ne kafin shi bisa shawarar lawyers ɗinsu.
           Ta gefe kuma ga jikin Ummie da ya rikice. Ga kuma Samraah dake asibiti har yanzu ba’a sallamota ba itama, sai dai wata irin kulawa take samu ta musamman da tattali a wajen Hajiya ʙarama har Mama Balki ta fara shan jinin jikinta. Sai dai abinda Mama Balki bata sani ba ita kanta Samraah nazartar Hajiya ʙarama take sannu a hankali. Gefe kuma tana kaima ALLAH kukanta. Koda labari Mama Balki bata sanar mata da ciwon Ummie ba sai yau da Falak tai kiran wayar Mama Balkin, a lokacin ita kuma ta ɗan fita dan haka Samraah ta ɗaga. Har yanzu basu taɓa haɗuwa da Falak ba sai dai tana cin abincin gidanta kullum. Bata da lafiya ne tana fama da tsohon ciki shiyyasa bata zo tama dubata ba, sai dai sun gaisa ta waya har kusan sau uku. Yanzun ma sun gaisa cike da kulawa ma juna tamkar dama can sun san junan nasu, kafin Samraah ta sanar mata Mama ta ɗan fita ne, amma idan ta dawo zata faɗa mata sai ta ʙara kira.
         Daga can Falak tai murmushi da faɗin, ā€œOkay ba damuwa ALLAH ya ʙara lafiya, dama zanji ko yaya jikin Ummie ne dan na kira Yaya Hayat ashe garin sauri yama bar phone ɗin a gida, gashi yanda ya fita a hargitse duk na kasa nutsuwaā€.
             Ɗan jimmm nayi zuciyata na bugawa da sauri-sauri jin ta ambaci Ummie, da ʙyar na iya tambayarta ā€œUmmien Maash Mansion? Wani abu ne ya sameta?ā€.
         Batare data fahimci kan tambayar ba cikin damuwa muryarta na rawa ta ce, ā€œEh ita, kin san kwana biyun nan jikin nata duk babu daɗi, to yau dai da alama ya tsananta ne dan shima Yaya Hayat a rikice ya fita TJ ya kirashi. Wlhy ina tausayawa Ummie, da ace inada wata babbar dama akan baiwar ALLAHr nan abinda zan farayi shine tsayawa akan samun lafiyarta, amma muna gani an hanamu taimakonta. Wanda keda ʙarfin yin hakan kuma an kulle masa tunani gaba ɗaya, dan wlhy da ace Yaya Awwab basu shiga tsakaninsa da lafiyar baiwar ALLAHr nan ba da kowama yaci ubansa, ai sun san shi ɗin ba kanwar lasa bane har Baba prof ɗin da Paah ba iya tankwarashi suke ba. Amma ba komai ALLAH yana nan, watarana sai labariā€.
           Tuni ma ni ba fahimtar zantukanta nake da ʙyau ba, rawa sosai jikina ke mun, ga hawaye suna bala’in gudu a saman fuskata. Ashe shiyyasa duk jiya bai zo asibitin ba, yau ma haka. Ko Hayatu mai ʙoʙarin zuwa sama da sau uku yana kawo musu abubuwa jiya sai dare ya shigo ya duba ta. Abinci ma TJ ne ke kawowa. Amma Maash tun daren shekaran jiya da zai tafi take cemasa ya dinga duba mata Ummie da bata abinci bai sake zuwa ba, harta ʙullacesa ma ita da, da tunanin ya gama cin moriyat ganga zai yada kwautrnta, ashe abinda ke faruwa kenan…
          ā€œYa subahanallah Samraah! Wani abu ke miki ciwo ne? Ko tashi kikayi da ʙarfi kika fama ciwon?ā€.
        Mama Balki ce mai maganar nan a rikice. Ɗagowa nayi ina kuka mai tsanani dan shashshekar da nake tasa har fisga numfashina keyi. Lallashina Mama Balki ta shiga yi tare da bani ruwa tace nasha. Da ʙyar na amsa nai maʙwarwa uku, jikinta ta jawoni ta rungume, hakan sai ya taimaka min wajen samun nutsuwa na fara sassauta kukan. Kaina na a saman cinyarta tana shafa gashina ta ce, ā€œSamraahā€.
           Cikin dasashjiyar muryata na amsa mata da, ā€œNa’am Mamaā€.
       ā€œMike faruwa?ā€.
      Da ʙyar na iya danne kukan dake taho min na ce, ā€œMama Ummie. Ashe bata da lafiya amma shine babu wanda ya sanar minā€.
         Iska ta ɗan furzar cikin damuwa. Kafin ta ce, ā€œWaye ta faɗa miki?ā€.
        ā€œFalakā€.
    Na bata amsa ina sharce hawaye…….āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’†š’Šš’ˆš’‰š’•


    ……Kanta ta girgiza da faɗin, ā€œNi ban san sai yaushe bakin Falak zai iya dinga koyon shiru ba. Kiyi haʙuri an ɓoye miki ne saboda kema ga yanayin da kike ciki. Shekaran jiya ne Alhaji ʙarami ya shiga yana ʙoʙarin bata abinci shine fa kawai jikin ya rikice. Ta jimasa ciwo sosai a hannu da ʙyar aka iya fiddoshi a ɗakin, daga nan duk wanda ya shiga da duka take korosa, to yau kuma sai ta yanke jiki ta faɗi saboda kwana biyun nan bata ci bata sha rashin abinci jikinta yayi week. Amma ki kwantar da hankalinki zuwa yanzu sun ce Alhamdullah komai ya dai-daita. Dan Hayatu ma ya tabbatar min tana barci saboda drip ɗin da aketa ʙara mata.ā€
          Duk da na ɗan ji nutsuwa sai da na sake sharce hawaye, ɗan shiru mukayi kafin a hankali nace, ā€œMamaā€.
        Da kulawa ta amsa min da, ā€œNa’am Samraahā€.
            ā€œMama a yanzu sai nake ganin kamar shi yafi dacewa ma abinda ke tare da shi ya rabu da shi kafin a samu nutsuwar yima Ummie magani. Duk da dai wani abu ya jima yana damuna. Yanzu duk kuɗinsa ace gidan nan babu cctv camaras tako ina?ā€.
           ā€œTabbas gaskiya kika faɗa Samraah. Sai dai mun kwatanta hakan muma bai yiwu ba, a dalilin tsanar magani da Alhaji ʙarami yayi tun yana ʙaraminsa. Ko yaya ruwa ya surka wlhy bazai sha miki shi ba koda da kala ne. Shiyyasa yin maganinsa keda matuʙar wahala. Gashi kuma shi ba’a zaune yake ba waje ɗaya, duk yanda muka so fara bashi koda ruwan addu’a ne sai kiga abin ya zama shiririta. Ina da tabbacin kuma wanda ke wannan aikin kullum cikin sabuntashi suke bawai sun koma sun kwanta bane suma. Maganar camara kuwa ai Alhaji ʙarami yasha sakawa amma sai a wayi gari duk an ciresu. Har ɓoyayyar camara an saka a gidan nan amma kamar abin maita wlhy sai da aka cireta. Hakan na nufin koma su waye a biye suke, shiyyasa ma kikaga ina sake jin tsoron al’amarin gidan nan da mutanensa. Dan idan bana jikinka ba banga wanda zai dinga maka wannan bita da ʙullin ba a nesa da kaiā€.
         Baki na buɗe zanyi magana sai naji kamar amalar motsin tsayawar mutum a ʙofa. Shiru nayi bance komai ba, sai kuma kamar ance na ɗaga ido na hango inuwa ta jikin window. Magana Mama zatayi na wayance ina mai zame kaina da ga cinyarta na ce, ā€œMama barci nake ji. Dan ALLAH idan Nurse ɗin nan tazo kice bana son allurar nan ni nama warke karki bari tamunā€.
            Kallon mamaki da naga Mama namun yasa nai mata nuni da window da ido. Tuni ta ɗauki haske kasancewar dama a ankare take. Itama sai ta wayance ta shiga Ę“ar dariya da faɗin, ā€œJa’ira ai allurar nan sai an kaita har ʙarshe, bari ma Hajiya tazo zance ta sake ʙara miki kwana biyu kiyi digir dake yanda zamu koma gida da ʙarfinkiā€.
           Shagwaɓa na shiga mata da faɗin ni bana so. Itako tana dariya. Daga haka mukayi shiru. Kwanciya nayi zuciyata na faman kai-kawo. Tabbas lokaci yayi fa dazan dawo hankalina. Dan na fahimci in har shi bai fita a halin da suke sanyashi ba baiwar ALLAHr nan bazata taɓa samun ingantaccen lafiya ba. Domin sauʙi yana samuwa a gareta, sai dai yanayin kwan-gaba kwan-baya da ake fuskanta yasa al’amarin ke taɓarɓarewa. Idan kuwa har za’a iya hana cctv camaras zama lafiya to lallai waɗan nan mutanen ba ʙaramin shiri sukai ba. Suma kuma suna buʙatar a shirya musu yanda ya kamata. Dan dole wayo al’amarin yake buʙata da hikima kamar yanda suma suke komai ta cikin basiraā€. Wannan tunane-tunanen da hawayen da suka kasa barin idanuna ne suka haifar min da zazzaɓi mai zafi, gashi naʙi gayama Mama har bayan sallar isha’i. Dan da ʙyar ma nayi alwala saboda sanyin da nake ji. Ina idarwa na haye gado na kwanta tare da duʙunʙunewa cikin bargo. Sosai na gaji da zaman asibitin nan, fatana kawai ALLAH yasa yazo dan shine kawai zaisa a sallameni. Yan gidansu dai dama babu wanda ya sake zuwa sai Hajiya ʙarama da nake gani, ita kam kullum ne sai ma tazo sama da sau uku, sai daga baya na fahimci ai dan asibitinta ne shiyyasa itama muke yawan ganintan…..

             🩸🌟🩸

       Sosai damuwar halin da Ummie ke ciki a kwana biyun nan yasa bai sake waiwayen asibitin ba. Duk da kuwa wani sashe na hankalinsa na’a can ɗin. Sai dai rashin isashen lafiya shima dana lokaci ta sashi baiyi wani yinʙuri ba. Yau kuma zafi da ʙuncin da gidan ya masa matuʙa ya sashi ɗan kimtsawa bayan ya dawo sallar isha’i. Tun la’asar ya kora Hayatu gida dan haka shi kaɗaine a sashen sai Laalah da TJ dake leʙowa akai-akai duba shi shi da Shu’aibu amintaccen guard ɗinsa. Tsaff ya fito yana zuba mayataccen ʙamshin nan nasa tamkar ba dare ba. Tj da Shu’aibu na ganinsa suka miʙe da sauri, hakama sauran ma’aikatan gidan sai gaisuwa suke miʙawa. Hannu kawai yake ɗaga musu dan kwana biyun nan miskilawan ne a kusa. Da ga shi sai TJ da Shu’aibu sukai fitar dan hana sauran guards ɗin binsu yayi. Tj ke driving Shu’aibu a gefensa. Shi kuma yana baya zaune idanunsa akan wayarsa yana daʙila. Kicin-kicin fuskar nan take babu alamar ya taɓa sanin minene ma dariya.
         Cike da girmamawa TJ ya ce, ā€œBoss ina muka nufa?ā€.
        Shiru bashi da niyyar amsawa. Sai da ya mula dan kansa ya furta, ā€œHospitalā€.
         Cike da girmamawa TJ ɗin ya amsa masa tare da ɗaukar hanya. Har sun gota wani bakery yace TJ ɗin ya dakata. Tuna duk lokacin da zasu je asibitin tare da Hayatu sai ya sa an tsaya ya sayi wasu abubuwan ya sashi cewa a dakatan. Shima TJ ɗin tun bai furta ba ya fahimci abinda yake nufi tunda dai koda yaushe da shi ake zuwa asibitin shima. Fita yayi zuwa cikin bakery ɗin batare daya amshi wani kuɗi ba, dan boss ya wuce fiye da haka a wajensu ai. Bai wani jima ba ya fito ɗauke da ledoji masu ʙyau har guda uku. Booth ya buɗe ya sakasu sannan ya dawo cikin motar. Zuwa yanzu ba wayar yake daʙila ba kansa ya kwantar a jikin kujerar ya lumshe idanunsa. Koda suka iso ma sai da ya ja kusan mintuna biyu tamkar mai nazarin ta yanda zai shiga cikin asibitin sannan ya fito. Yana gaba cikin takun nan nashi na ʙasaita da isa su TJ na biye da shi. Babu yawaitar mutane har ma ma’aikatan jefi-jefi ne. Ko kallon wanda suke a reseption ɗin kuwa baiyi ba yayi wucewarsa. Sai su TJ ne suka gaishesu. Suko suka bishi da kallo tamkar wasu tsoffin mayu. Sai faman washe bakuna suke yau gasu ga Maash, mutumin da yafi kuɗi wahalar gani a Nigeria. Dama wasu a abokan aikinsu sun sanar musu da zuwansa a kwana biyun nan, sai dai su basu taɓa cin karo da shi ba sai yau ɗin…

    Har yanzu duʙunʙune nake a cikin bargo ina rawar sanyi dan zazzaɓi nake ji sosai. Ga hawayen damuwa da halin da Ummie ke ciki sun kasa tsayawa a idanuna. Ita mama Balki ta ɗauka nayi barci ne, dan haka ta maida hankalinta a kallon tv tana sauraren wa’azin malam Ali isa fantami da aka saka a African tv3. Knocking ʙofa da akayi a hankali kamar abin dole ya sata rage ʙarar tvn, shiru kamar baza’a sake ba sai kuma aka ʙara. Miʙewa tayi zuwa jikin ʙofar tana tambayar waye? Jin ba’a amsa ba ta buɗe. Ni dai duk ina jinsu amma da yake har kaina na’a cikin bargo ba ganin komai nake ba.

         Murnar da naji tana yi da ambaton sunan Alhaji ʘarami ya sanya gabana faɗuwa. Sai ko ga mayataccen ʙamshinsa ya gama isowa har cikin hancina. Wasu muryoyi biyu naji suna gaisheta da tambayarta mai jiki. Na gane muryar driver ɗinsa. Ɗayan ne dai ban gane waye ba amma nasan ba hayatu bane ba. Sai da naji alamun fitarsu da rufe ʙofa sannan shima naji muryarsa a daʙilen nan can ʙasa-ʙasa kamar abin dole yana gaida Mama. Ita ko da kulawa take amsa masa da tambayarsa jikinsa da kuma na Ummie. Nan ɗin ma da ʙyar ya amsa itama yana tambayarta ya mai jiki. Itako da fara’a ta ce masa, ā€œA jiki da sauʙi sosai. Yau ne ma ta so birkicewa saboda samun labarin jikin Ummie daya motsa da tayi. Dan har bayan sallar magriba ɗin nan tana shartar hawaye sai da na ɗan mata nasiha sannan tai shiru, inaga shine ma dalilin kwanciyar da wuri sai kuma barci ya ɗauke ta. Banji yace komai ba, sai dai haka kawai na dinga jin kaifin idanunsa a jikina. Shiru ɗakin na kusan minti ɗaya sai kuma naji ʙarar buɗe ʙofa da rufewa. A zatonta shine ya fita, dan haka cike da shagwaɓa na janye bargon daga saman fuskata zanyi magana da Mama. Zuuuu naji jinina na falfala uban gudu ta cikin jijiyoyina tsabar shock ɗin cin karo da abinda nai zaton shi ya fita. Da sauri na kauda kaina na sake maida fuskata cikin bargon.
            A bazata naji alamar an zauna a kusa da ni, Ji nai na sake daburcewa kamar zan fasa ihu, amma sai na dake tare da yin luff a cikin bargon ina addu’ar ALLAH yasa kada yace sai na buɗe kaina……..āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’š’Šš’š’†

    ……Shiru ɗakin har na fara murna. Kusan mintuna uku muna a haka babu motsin komai sai naji yayi ɗan gyaran murya. Idanuna na sake rumtsewa da ʙarfi batare da na yarda na motsa ɗin ba dai. Sake yi yayi, nan ma naʙi na motsa, sai da yay ta uku sai kuma a hankali ya ɗaura da faɗin,
          ā€œDama Ummie c….ā€
        A zabure na yaye bargon gaba ɗayansa. Na ware dukan girman idanuna a kansa. Lips ɗina na rawa a marairaice na ce, ā€œUmmie mi?ā€. Maimakon amsa min sai kafe cikin idanuna yayi da nasa cat eyes ɗin masu matuʙar girma da yalwar gashi. Wani irin tashi tsigar jikina tayi, sai kif-kif kawai nake faman yi da idanu. Sai faman kokawa nake da numfashina dake seizing.
             ā€œStubborn girlā€.
        Nakasashiyar muryarsa ta daki cikin kunnena duk da kuwa cikin low voice yayi ta, badan ma idanuna na akansa ba babu yanda za’ai na jisa dan pinkish lips ɗinsa ne kawai suka motsa a hankali. Kamar wata sakarai na jujjuya masa kaina a hankali. Motsa lips ɗina dake Ę“ar rawa na shiga yi, da ʙyar na iya haɗa kalmar, ā€œMi ya sa mu Um mie?ā€ a rarrabe ina rissinar da idanuna da suka ciko da hawaye. Dan duk yanda na ʙudirci masa tsiwa ko kallon cikin idanunsa nayi magana sai naji sam na gagara yin hakan. Mutum ne mai masifar kwar jini da cika wuri. ALLAH ya azurtashi da wani irin girma a gaban duk wanda ya tsaya koda ace ya fisa a shekaru da matsayi. Saukar tattausan tafin hannunasa saman fusakata ya sani sake ɗago idanu da sauri na kallesa. A cikin nashi cat idanun suka sake faɗawa. Kallon juna muke a wani irin yanayi har na tsawon shuɗewar wasu sakanni. Kafin a kasalance na motsa nawa dake tara ʙwallan da ban san na minene ba. Shi ko har a lokacin kallon nawa yake yi batare da ya ʙyafta ba, sai ma cikin wani irin soft voice and silent and slowly ya furta, ā€œShe is missing you, and she need youā€.
            ā€œI miss her tooā€. Na faɗa nima a hankalin ʙwallar data cika min idanu na gangarowa. Idanunsa ya sake ɗan lumshewa tare da buɗewa a lokaci guda ya cigaba da kallona ina kuka sosai harda shashsheka. Shi bai lallasheni ba, bai kuma janye hannunsa dake a kan fuskata ba har yanzu. Tsawon mintuna biyu ina kukana, dan shirunsa sake tunzurani yake. A bazata matuʙar bazata cikin low voice ɗin sa ya furta,
          ā€œSamrhā€.
       Cak na tsaya da kukan da nake, tare da ɗago jiʙaʙʙun idanuna na kallesa. Kallon nawa shima yake da shanyayun nashi da suka canja launi zuwa golden an blue.
            ā€œWhy are you crying?ā€.
         Ya sake faɗa muryarsa na sake komawa can ʙasan maʙoshi. Samun kaina nayi da sake sakar masa sabon kukan. Tare da riʙo hannunsa dake akan fuskata na ʙan ʙame.
          Idanunsa da suka gama canja launi kawai ya zuba mata. Sai Adams apple ɗinsa ne ke faman kaiwa da komawa a cikin maʙoshinsa. A hankali ya kai ɗayan hannunsa saman kafaɗarta, riʙota yayi tare da ɗagota gaba ɗayanta batare da ya janye hannun nasa data ʙanʙame ba sai da ya kaita gab da jikinsa sannan ya janye ya turata cikin jikin nashi gaba ɗayanta. Tsam ya rungumeta yana mai lumshe idanun nasa ʙam-ʙam shima saboda zafin da jikinta ya ɗauka duk da da akwai kaya a jikinsu su duka sai da ya bala’in ratsashi.
             Ni kam jina a jikin nasa ya sakani sake fashewa da kuka. A hankali na fara ɗan dukan bayansa ina faɗin, ā€œWhy! Why? Why? Suke wahalar da rayuwarta? Mita musu da zafi haka? Da ga ganinta She is an innocent and strong woman. Basu barta haka ba, sun rabata da ku jininta da zata ji sanyi a wajen ku. Natsane su, wlhy na tsanesu. I promise my self sai na ɗaukar mata fansa koda zasu maidani fiye da yanda suka mata. Sai na sakasu gudun ceton rai da babu mafaka Ya Awwab. I promise….ā€
         Kuka ya sake sarʙeta. Sai wani irin jan nunfashi take a sarʙe kamar mai ciwon asthma. Da sauri ya rabata da jikinsa, tare da kwantar da ita a kan cinyarsa. Sosai numfashin nata ke fisga, hannayensa ya saka duka biyu a kumatunta ya shiga ɗan bubbugawa da kiran sunanta.
             ā€œSamrh! Samrh! Please keep calm. I know you can, please calm down. Hundred percent I am with you.ā€
          Ina da gaske ʙoʙarin ʙwacewa numfashin nata yake. Ai baima san ya figi bottle na ruwa dake a side drawer ba ya zuba a hannu ya shafa mata duk da kuwa tana numfashi, sai kuma yay saurin kai mata ruwa a baki amma bakin ya gama datsewa ruwan yaʙi shiga. Da sauri ya kai kan nasa bakin ya zuʙa, batare da wani tunani ba ya ranʙwafo kanta ya ɗaura lips ɗinsa a saman nata ya shiga juye mata ruwan tare da riʙe hancinta. Wani masifar jan nunfashi tayi ta baki sai gashi ta zuʙe ruwan gaba ɗaya. Hancin nata ya saki tare da janye bakinsa. Ita kuma ta fara tari sosai. Sake ɗagota yayi a hankali ya maidata jikinsa ya rungume suna sauke ajiyar zuciya a tare. Sunfi mintuna uku a haka sai da ya tabbatar zuciyarta ya gama sauka sannan ya raba jikinsu ya kwantar da ita a gadon a hankali…
               Kasa buɗe idanuna nayi, sai ajiyar zuciya kawai nake saukewa a jajjere. Jin saukar abu mai taushi da ʙamshi a saman fuskarta ya sani buɗe idanuna a hankali. Shine ke goge min hawaye da farin handkerchief ɗinsa tass. Idanunsa ya saka cikin nawa har ya gama. Batare da ya janye handkerchief ɗin ba da ɗan yanayin lumshe idanu da buɗewa ya furta, ā€œMiyasa fitina baya miki wuya? Samrh! Ba’a gaggawa a al’amarin maʙiyi, idan ba haka ba zai fika gudu ne wajen cimma manufa. Lokacin da zaka isa sai ka samu shi har ya gama ya juyo. Be a gentle okayā€.
         Sosai zantukan nasa suka shigeni tare da canja min wasu tunanina da yawa a kansa. Cikin suɓutar baki muryata a dusashe na furta, ā€œKana nufin kaima duk abinda ke faruwa kana sane?ā€.
            A bazata naga ya wani ɗan taɓe gefen small pinkish lips ɗinsa da lumshe idanunsa sannan ya saki murmushi. Bily idan nace miki kaɗan ya rage zuciyata ta ɓaro akan murmushin nan nasa da salon da yayisa ki yarda da ni kawai. Badan yafi kowa iyawa bane, sai dan murmushi ya kasance ba ɗabi’arsa bace. Amma tabbas magana ta gaskiya murmushin ya ɗebeni iya ɗiba. Dan kaɗan ya rage na fallasa ɓoyayyen al’amarin da na jima ina binnewa a kansa.
          (Kin sani a duhu mutuniyar, kodai kin jima kina son Maash ne?).
         ā€œHummm Bily kenan abar dai zancen sai lokacin yinsa yayiā€. Na faɗa cikin Ę“ar dariya.
        (Lallai kam, to shike nan na bari muje zuwa labari).

           Yanda yay murmushin har ban san na kafesa da mayataccen kallo ba.  Idanunsa ya ɗan waro min waje da ɗagesu alamar kallon fa?. Cikin sauri na kauda fuskata gaba ɗaya ina tura baki da faɗin, ā€œMiye abin kallon ma ananā€.
           Bai tanka min ba, sai ma ɗan kauda kansa da yay gefe. Banyi zaton jin shirunsa a wannan gaɓar ba. Amma nima dai sai na basar kawai tare da ture hannunsa na janye sauran jikina dake a nasa tare da jan bargo na juya masa baya. Dan in banyi hakan ba akwai babbar matsala, dan komai zai iya fitowa saboda yanda zuciyata ke bugawa da sauri-sauri abinda ke can ʙasanta a ɓoye na azalzalota.
           Shiru ban sake jin motsinsa ba. Ban kuma yarda na kallesa ba har fin mintuna biyar. Sai a lokacin naji motsin buɗe ʙofa, ɗan juyawa nai kaɗan. Sauka idanuna sukayi akan bayansa dai-dai yana ʙarasa ficewa da jan ʙofar ya rufe a hankali. Nima lumshe idanuna nayi ina sauke ajiyar zuciya. Sai kuma na sake dunʙule jikina a cikin bargon dan ji nake kamar zazzaɓin na ʙaruwar min ma. Mintuna bai fi huɗu da wasu sakanni ba aka sake buɗe ʙofar, idanun na sake buɗewa a hankali. Yanzun kam Mama Balki ne da Doctor sai shi a ʙarshen shigowa. Hannayensa duka biyu a cikin aljihun baʙin wandonsa. Idanun na maida kawai na rufe, dan nasan bai wuce akan zazzaɓin jikina yaje yayo min wannan gayyar ba.

             🩸🌟🌟🌟🩸

      A hankali take faman kaiwa da komawa a cikin ɗakin nata kai kace safa da marwa take ko motsa jiki. Sai dai sam ba haka bane. Abubuwane masu yawa ke matuʙar damunta da cizar mata zuciya. Dan tun zaman da sukai da Yallaɓai ɗazun da magrib ta gagara samun sukuni. Gaba ɗaya taji ta kasa komawa asibitin da taci burin komawa dan akwai wani baʙo da zatai mai muhimmanci. Maganganunta da Yallaɓai ne suka shiga dawo mata dalla-dalla tamkar a yanzu suke tattauna su....

        ā€œYaushe yarinyar nan tazo aiki gidanku? Waye kuma ya kawota?ā€.
              ā€œLokacin muna Dubai muma zuwa kawai mukai muka sameta anan. Amma ance Mashi’a ce ta kawotaā€.
          ā€œMashi’a?!ā€.
        ā€œYes ita fa. A cewarta kuma ta kawota ne as a birthday gift wa mahaukaciyar matar can. Tunda masu aikinta sun sake guduwa a lokacin babu mai kula da itaā€.
         ā€œA ina ta ɗakkota?ā€.
       Ɗan jimm tayi, sai kuma ta ce, ā€œGaskiya wannan ne ban sani baā€.
           Kasa sake cewa komai yayi, sai ma kai-kawo daya shiga yi hannayensa goye a bayansa……….āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’†š’


    …….Yayi kusan sau fin huɗu sannan ya dawo ya zauna. Cikin kaushin murya da dakewa ya furta, ā€œDole ne yarinyar nan ta mutu a asibitinki. Kuma a yau zuwa gobe nake buʙatar sanin daga inda ta fito? Miye dalilin Mashi’a na kawota?. Zaki cigaba da riʙeta har zuwa kwanaki uku da za’a gama min bincike naā€.
        Idanu Hajiya ʘarama ta zubama mutumin zuciyarta na gudu da sauri-sauri a ʙirjinta. Cikin ɗan rawar lips muryarta na seizing ta ce, ā€œAmma yallaɓai hakan fa zai iya zama kuskure. Dan yarinyar nan gaba ɗaya komanta ya gama dai-daita raunin daya jimata ne kawai ya rage ya ʙarasa warkewa mu sallameta zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu ko jibi. Sannan case ɗinta bama fa a hannuna yake ba doctor Larai ce ke kula da ita. Daɗin daɗawa Awwab. Yaron nan fa ya wuce duk inda kake zato da tsammanin sa kaima ka sani. Ni wlhy zuciyata ma ta fara bani kamar a ankare yake da abubuwa da yawa. Gashi sam baya jin tsoro ko shakkar kowa. Yanzu ka dubafa yarinyar mutane yama fyaɗe a cikin gidansu amma komansa bai canja ba face ma wani irin kulawa da yake bata ga girman kai sabo da yake ji da sam na gagara fassara al’amarin nasuā€.
             ā€œMtsooww Lawusa, ke kin san dai idan na faɗi magana ko zartar da hukunci bana canjawa ko? Dukan waɗan nan hujjojin naki basa gabana. Gawar yarinyar nan kawai nake buʙatar gani fine and doneā€. Ya ʙare maganar a wani irin hankali yana zazzaro mata idanunsa da sukai mugun kaɗawa saboda giyar da yake ta faman lodama cikinsa tun kan tazo. Yawu masu kauri ta haɗiye. Sai kuma ta shiga jinjina kanta. ā€œOkay shike nan naji zan kashe yarinya bayan ansan wacece. Sai dai fa kaima ya kamata ka tuna lokaci yayi da zaka yi komai a wuce wajen. Nifa ina buʙatar shares ɗina, dan lokaci yayi da zan mora wahalata ta shekaru gaskiya. Tunda ba ʙuruciya nake ʙarawa ba. Yaron can Fahad banga amfanin saba ai, shima ya cancanci mutuwa. Sannan magana ta gaskiya mahaukaciyar matar nan na gaji da shiga da fita ina shan warin sashen ta itama. Ya kamata kayi wani abu, dan nasan dai zuwa yanzu kaima ka fanshe dukan alʙawarinka da alwashinka a kanta. Kaga sai muje next target wato Awwab. Dan Doctor Ram ya tabbatar min ko a yau muke son poison ɗin nan a shirye yake da aiko mana shi Nigeria.ā€
              Iska mutumin da tunda ta fara maganar ke kallonta yake ta faman furzarwa. Sai da ta kai har ʙarshe kafin ya ɗauka kofin giyarsa ya kai baki, ʙarasa shanye wanda ya rage a ciki yayi ya dire glass cup ɗin a saman Centre table ɗin gabansa yana wani girgiza kansa. Sai kuma ya maido jajayen idanunsa ya zuba mata. ā€œDont warry Lawusa. Komai da kika sani a tsare yana nan bai canja ba. Sai ma ʙarin shares da kowannen mu ya samu sakamakon sake hauhawar dukiyar nan. Dan yaron nan ba ʙaramin mahaukacin arziʙi ya tara mana ba. Shiyyasa nake son ki fahimceni akan kashe yarinyar nan. Dan sam na kasa jin nutsuwa akan barinta raye tun kan nasan wacece ita. Kije ki ʙarasa aikin ki a next zama zaki ji mina tsara game da Fahad ɗin shimaā€.
            ā€œShike nan yallaɓai ALLAH ya ʙara lafiya da nisan kwana. Na barka lafiya a huta gajiyaā€.
         Hannu kawai ya ɗaga mata da maida idanunsa luuu ya rufe cikin mayen barcin buguwar da yayi……

         Iska ta furzar mai zafin gaske. Tare da tura hannunta cikin hular kanta. A take hular ta zame ta faɗi, gashinta mai ʙarancin tsayi da cika ya bayyana. Bata damu ba, dan abinda ya dame ta shi ya dameta. Tunda ta haɗu da Yallaɓai bai taɓa saka mata doka ko sanyata aiki ta gagara yinsa ba, saboda ra’ayinsu bai taɓa banbanta ba. Sai dai a wannan gaɓar an samu akasi. Dan yallaɓai ya sakata yin aikin da ita kanta tasan idan tayisa sai ta cutu. Matuʙar cutuwa. Domin kuwa ita kaɗai tasan irin son da takema yarinyar nan with all her heart. Duk da tana jin zafin abinda shegen yaron nan mai kama da ɗanyen attaruhu yay mata ɗigon sonta bai ragu a zuciyarta ba. Jinta take a yanda ta jure kwanakin baya akanta yanzu bazata iya ba. Dan wani irin mayataccen buʙatar son kasancewa da ita takeyi. A jiya kaɗan ya rage tabi dare a asibitin ta lalubeta. Sai dai ba haka take so ba. Tafi son su mori juna yanda ya kamata. Dan tana jinta a ranta banban da sauran waɗanda ta mu’amalata daga fara wannan harkar zuwa yanzun. Yarinyar akwai kayan marmari fresh a jikinta matuʙa da har wani sashe na zuciyarta na ʙin ganin bebekin Awwab akan abinda yay mata. Yo ita mace ma ta kasa nutsuwa balle shi namiji mai ji da shekarun ʙuruciya da hutu. Sosai tana jinta a tsaka me wuya…
             ā€œYau ma wani ɗinne ya mutu da kika kasa nutsuwa?ā€.
        Firgigit ta dawo hankalinta tare da juyawa tana kallonsa. Shima kallonta yake fuska babu yabo babu fallasa. Paah ya sake watsa mata kallo murya a kausashe ya furta, ā€œDan iskanci kinzo nan kin shanyani bayan ina can ina jiran ki kawo min coffeeā€.
          Ajiyar zuciya Hajiya ʙarama ta sauke da ʙoʙarin controlling kanta. A hankali ta saki murmushi tare da canja yanayinta like she is innocent woman, cikin kwantar da murya ta ce, ā€œKayi haʙuri Abban Awwab. ʘafata ce fa ta riʙe daga fitowa a bayi shine nake ɗan mammotsata. Amma wlhy kana raina tunda naga lokacin shan coffee ɗinka yayi. Amma ganin baka kirani ba yasa nai tunanin ko baku dawo daga masallaci baneā€.
             ā€œTunda nine limamin masallacin baā€.
         Ya faɗa a gatsine cike da sake tunzura. Sake kwantar da murya tayi da shiga bashi haʙuri. Uffan bai sake cemata ba ya fita fuuuu yana harare-harare dan dama borin kunya ne kawai ya naɗe da hauka. Tun ɗazun yana a garden ɗin Maash tare da Siyama suna holewarsu. Dan tunda ya fahimci Maash baya gidan ya tura mata saʙo a waya kan ta samesa a garden ɗin Kasancewar yasan anan ɗine zasu iya zama safe fiye da ko’ina a gidan irin wannan lokacin. Sai yanzu ne yake fitowa dan yasan duk inda Awwab yake yana gab da dawowa gidan….
          Itama da kallon harara ta bisa. Kafin taja tsaki da faɗin, ā€œNadai kusan yarda ʙwallon mangwaro na huta da ʙuda stupid man. Dan ɗauke beauty yarinyar nan zanyi mubar ʙasar zuwa can muyi aurenmu mu more rayuwar mu. (Umarnin yallaɓai fa?) Zuciyarta ta ayyana mata. Kanta dake wani irin sara mata ta dafe kawai zuciyarta na bugawa da sauri-sauri. Lallai dole ne tasan mafita a daren yau basai gobe ba. Dan tafi kowa sanin wanene yallaɓai akan duk abinda ya sa gaba. Amma bari taje ta bama wannan sakaran coffee dai ta dawo…..

          (Tofa šŸ¤” kaji kuma wani lissafin 🄱🤫)

            šŸ’¢šŸŖ“šŸ’¢šŸŖ“šŸ’¢

        A gidan Abba Imamu rayuwa ta matuʙar juyama Mom baya. Dan sam ta kasa gane komai akan al’amarin Halime. Yarinya ce shu’uma matuʙa. Ga kalolin baʙin ciki da take tura mata iri daban-daban. Yanzu har takai Abba ya sallami mai aiki yace kowa tai aikinta ranar girkinta. Mom son jiki, Bibaa da Baby basu iya komai ba. Sai yazam a gidan duk ranar aikin Mom yini ake da yunwa, dan ko anyi abincin da wahala ya ciyu. Daga ʙarshe su ʙare da rigima ita da Abba. Dan ya tabbatar mata shi kam bazai ɗauki wannan banzan halin ba da almabazarancin abinci. Ashe da can duk wahalar gyaran gidan da abinci dama Samraah ce keyi ita kaɗai nata Ę“aĘ“an na kwance. To ta sani bata cutar masa ɗiyar Ę“ar uwa ba kanta ta cuta. Dan ba baki ya mata ba Ę“aĘ“anta in har a haka zata kaisu gidan miji to ta shirya kuwa za’a dinga koro mata su. Wannan magana tasa ta ʙona mata rai a ranar sai da suka tafka rigima sosai data kaisa da bata wan shika. Aiko dai tace babu inda zata. Kota kanta baibi ba yay ficewarsa.
          Sam Halime bama tasan abinda ke faruwa ba ita. Dan kwanakin nan gaba ɗaya bata ganema kanta. Kullum bata da aiki sai barci, itama dai aikin gidan a ranar girkin nata ʙarfin hali kawai take yi wajen yinsa. Sai yamma taji zazzaɓi yace salamu alaikum. Bazata taɓa samun nutsuwa ba sai irin sha ɗayan nan na dare. A yau ɗin ma da aka tafka rigimar har ya bama Mom sakin tana barci bata san bikin da akeyi ba. Amma mi, Bibaa da Baby na ganin Abban ya fita suka afka ɗakin Halimen wai zasu daketa. Sun san itace ke ʙullama Mom ɗinsu munafunci. Miye-miye dai magana tsaff a bakunansu. Cikin barci kawai Halime taji an sauke mata uban dundu. A firgice ta farka tare da sakin ihu. Sai kuma ta tsaya cak ganin Bibaa da Baby tsaye kanta suna huci. Kallon mamaki ta bisu da shi, sai kuma ta tashi da ʙyau cikin dakewa ta tambayesu ko lafiya?.
            ā€œUwarki zamu ci, shegiya annoba. Wlhy yau sai mun miki jina-jina a gidan nan dan ubankiā€.
          ā€œTofa babbar magana, wai kishiya taga abin cikin zanen kishiyartaā€. Halime ta faɗa tana yayimar ɗan kwalinta ta aza bisa kai tare da sakkowa a gado. Waya ta ɗauka tana cigaba da faɗin, ā€œAi ku jira bani kaɗai ya kamata ku cima uwar ba, dole na kira Imamu kamar abin zaifi armashi. Kunga sai ku tuɓe ʙaton banza ku haɗamu ku lakaɗa mana dukan tsiya tunda shine ya kawoni gidanā€.
         Sororo Baby da Bibaa sukai suna kallonta. Kafin cikin ʙarfi hali da tsiwa Bibaa ta ce, ā€œBadan Abbanmu ne ʙaton banza ba dan ubanki. Sai dai idan kece ʙatuwar banza. Kuma wlhy yau sai kin ban mana gidanmuā€.
             Dariya sosai Halime ta sheʙe da shi, kafin ta riʙe haɓa da faɗin, ā€œOh ni Halimatu. Gidanku dai gidanku dai. To ke banda abinki Habi wace sakarar mace ke alfahari da gidan tsohonta? Ai macen data kai mace gidan mijinta take ma fata da alfahari, dan acan ne idan ta tadda komai rigijif-jif-jif sai kiga ta gyara gidansu albarkar iyaye ta bata tsaro tako ina. Dan haka riʙe cika bakin nan naki wannan gidan Halime ne da Jalilah, Habi dai har yanzu bata da gida sai na raɓe-raɓe. Garama ita wannan galwalin ta kusa shiga daga cikiā€. Tai maganar tana nuna Baby..  
            Cikin fusata Baby tace, ā€œWaye Galwali? Aiko yau sai na tabbatar miki na fiki hauka da tashanciā€. Fuuu tayo kan Halime…….āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’†š’š’†š’—š’†š’

    ……Kafinma ta kai hannu kanta ita ta ɗauke fuskar Baby da maruka. Ta shaʙo wuyan Bibaa dake bayanta itama ta bata nata. Basu gama dawowa a hayyacinsu ba ta shiga musu dukan kan mai uwa da wabi. Yo har a gayawa Halime iya danbe. Ita da ake kira giwar dambe a wajen ɗibar ruwa a garinsu. Kai hatta a islamiyya duk wanda ya sake ta haɗosu da Halime aka haɗu a lungun kaci uwaka bayan an tashi to ranar kuwa sai yaci uwar tasa. Cikin ʙanʙanin lokaci ta musu lis da duka. Sai gasu a ʙasa suna faman ribzar kuka. Itako ta ɗauki sabuwar wayarta da Abba ya siya mata kwanan nan tayi kiransa tana kuka wai yazo gasu Baby da taɓare zasu bigeta.
         Bawan ALLAH sai gashi a haukace harda Alhaji Sadisu. Suka ko sameta kwance tana ɗan nishi ita adole ga wadda taci duka. Gashi ta kawo jan baki ta ɗan sassaka a wasu wurare na fuskarta da hannu wai duk sayin duka ne. Abinka da fara saika ɗauka haka ɗinne. Ido rufe Abba ya dinga sauke musu maruka abinda bai taɓa koda kwatanta yi ba. Sai dai ma idan Mom ta zugashi akan Samraah yana mata faɗa ita yana marinta suna dariya. Haukace masa Mom tayi da kuka da ihu, amma ada idan ta zuga aka mari Samraah daɗi take ji, ya kuma tabbatar mata idan har ta matso shi sai ya ʙara tsinke igiyar aurensu data rage. Dole taja birki tana kuka sai Alhaji Sadisu ne ya amshesu da ʙyar. Amma sai da yay musu lilis da duka ga wanda Halime tayi musu. Ya kuma tabbatar da ya matso da auren Baby nanda ranar juma’a ko daga shi sai mutanen anguwa ne za’a ɗaura ta tafi haka dan ta ishesa. Itama kuma Bibaan idan bata kama kanta ba zai aurar da ita ga duk wanda ya masa babu abinda ya shallesa da wani karatunta. Haka suka dinga kuka. Shiko ya kama Halimensa sukai ɗaki yana lallashi. Sai dai ita kuma duk jikinta yayi sanyi, dan harga ALLAH batayi zaton zai dakesu haka ba. Ita kawai tayi ne a tunaninta faɗa kawai zai musu a wuce wajen. Koda suka shiga ɗaki sai ta kasa haʙuri ta fito ta sanar masa gaskiyar abinda ya faru harda dukan datai musu. Tama nuna masa video data ɗauka dan sanda tace zata kirashi da farko bashi ɗin ta kiraba ashe video tajeyi.
          Wannan halin nata shine abu na farko da yake sakashi jin ʙaunarta fiye da koda yaushe. Dan a ɗan zamansu sam ya fahimci Halime bata iya ʙarya ba. Sannan bata taɓa kawo masa ʙarar Mom ta mata wani abu a gidan ba idan baya nan kosu yaran sun mata. Sai dai ita Mom ɗin ta tonama kanta da kanta asiri ta hanyar gaya masa. Shiyyasa yau data kirashi ya taho a rikice. Amma Mom wani lokacin ma tun suna rigimar take kiransa ta sanar masa ʙarya da gaskiya cikin kunfar baki. Idan ya dawo gida yana jiran yaji Halime tace wani abu sai yaji shiru, ko yama samu tana firinfijimarta a gidan hankali kwance tamkar komai bai faru ba. Dan ita in har akwai wuta tv na kunne shikenan tace bata da sauran takaici a duniya. Balle ta haɗa uban shayinta cikin ʙaton kofi da burodi ta soya ʙwai ta zauna tana sha tana kallo ai ji take duniya babu ya ita. Har da rana da yamma shan shayi take saboda masifar ʙaunarsa da takeyi tun tana ʙaramarta. Abinci ma bai cika damunta ba in dai akwai shayi da burodi balle ga madara a ciki yaji da sauran kayan shayi ace kuma akwai soyayyen ʙwai wayyo jinta take kamar a aljanna. Yasha gwadata akan magana da Mom take sanar masa game da ita. Amma mutuniyar sai ta basar tama nuna ita yaushe akayi hakan, idan ma anyi to ta manta. Koda yake harga ALLAH bawai tanayi don makirci bane ko wani abu. Kawai ita har cikin ranta da halayenta da anyi abu ya wuce shikenan kawai sai wani ya taso kuma. Wannan dai ta gama da babinsa. Idan ko har kakaga Halime ta riʙe abu a rai ya dameta to lallai al’amarin babbane matuʙa. Dan wahalar data sha a hannun innarta da ace tana riʙewa a rai da tuni hawan jini da ciwon zuciya sun kai rayuwar yarinyar ʙasa….

        ā¤ļøā€šŸ”„ā¤ļøā€šŸ”„ā¤ļøā€šŸ”„ā¤ļøā€šŸ”„ā¤ļøā€šŸ”„

             ʘarfe sha ɗaya da wasu mintuna suke shigowa gidan. Har gaban dashensa TJ ya faka motar, da sauri Shu’aibu ya fito ya buɗe masa. Koda ya fita maimakon shiga sashen nasa sai ya koma ainahin ʙofar shiga babban sashen gidan. Babu kowa a falon sai Azizat dake dakon jiran dawowarsa. Yana shigowa kuwa ta miʙe zambar. Fuskarta ɗauke da murmushi ta nufosa tana masa sannu da zuwa cike da shagwaɓa. Sai da tazo gab da shi ya wani watsa mata mummunan kallo yayi wucewarsa upstairs. Kai tsaye sashen Ummie ya nufa ya barta nan tsaye baki sake tana binsa da kallo ga hawaye na gudu a fuskarta. Sai kuma ta kwasa da gudu tai sashen Hajiya Mammah itama. Sai dai tana murɗa ʙofar bedroom ɗin ta tajita a rufe gamm. Jingina tayi jikin ʙofar tana sake fashewa da kuka. Sai kuma wani ɗan nishi-nishi da take juyowa kamar daga cikin bedroom ɗin ya sata fara sassauta kukan nata tai tsai alamar saurare. Tabbas daga ɗakin mahaifiyar tata ne. Knocking ʙofar ta farayi da kiran sunan ta amma babu alamar za’a buɗe, sai dai kamar anyi shiru an daina nishin. Sake fashewa tayi da kuka tare da barin jikin ʙofar da gudu tai ɗakinta.

         Wata shegiyar dariya Arwa dake laɓe tun ɗazun tana kallonta dan komai akan idonta ya faru ta saki, sai kuma cike da farin ciki ta furta, ā€œIska na wahalar da mai kayan karaā€ ta juya cike da takun girgiza jiki ta koma nata ɗakin dake a sashen uwarta Hajiya ʙarama. Dan su dukansu kowanne a sashen mahaifiyarsa yake har suma su Malika….

           ā˜… A ɓangaren Maash kuwa bai wani jima ba a sashen Ummie ya fito, dan ya samu tana barci ne alamar sauki na samuwa. Baya buʙatar wata matsalar ta sake samuwa a dalilin shigowar tasa dan haka ya juya ya fita a kan lokaci. Har zai wuce sai kuma yay tunanin shiga sashen Paah dan akwai maganar da yake sun suyi. Gobe in ALLAH ya kaimu kuma ya sanar masa da baʙi da zaiyi da wuri zai fita a gidan ba lallai su haɗu ba. Sashen Paah ɗin ya nufa da tunanin shi kaɗaine dan yasan da wahala Hajiya ʙarama idan tana a gidan kasancewar ya ganta a asibiti ɗazun. Knocking yay har sau biyu amma baiji motsin komai ba. Yasan Paah da kallon labarai yanzu haka hankalinsa nacan baima jisa ba. Dan barci dai yanada tabbacin baiyisa ba zuwa yanzun kam. Kansa tsaye ya tura ʙofar ya shiga kawai, sai dai kuma da saurin tsiya ya tsaya cak dai-dai yana ɗaga kafarsa zaiyi taku kusan na biyar a cikin falon sakamakon furucin da Paah ɗin yayi waya a kunnensa. Da ʙarfi yaja numfashinsa da ke neman fisgewa daga cikin ʙirjinsa. A wani irin harzuʙe da kaushin harshe ya furta, ā€œPaah!!ā€.
           A bala’in rikice Paah ya juyo tare da sakin wayar ʙasa yan zazzaro idanunsa. Fuuuu Maash ya juya ya fice a falon tare da bugo masa ʙofar da masifar ʙarfi har sai da ya zabura. ā€œ Innalillahi wa-inna ilaihiraji’unā€. Ya shiga maimaitawa cikin tashin hankali. Shi ya haifi Awwab, amma wlhy zai iya rantsuwa da baya jin tsoron wani sama da yanda yake shakkar yaron nan. Kai hatta Baba prof daya haifesa baya jin yana shakkarsa kamar Muhammad. Koda wasa baya son Muhammad ya kamasa da wani laifi musamman akan abinda za’ace ya shafi mahaifiyarsa koda kuwa ɗan kaɗan ne…

           Sashen Maash ɗin Paah ya nufa a ɗarare cikin kuma tashin hankali, dan Gara yaje suyita kawai baya son ya ɗauki fushin nan da shi. Kasancewar ta ainahin ʙofar shiga sashen ya fita yabi kansa tsaye ya shiga. Shu’aibu ya samu a falo da TJ. Cikin girmamawa suka shiga gaidashi. Da ʙyar ya iya danne yanayinsa ya amsa musu. Kafin ya ɗora da tambayar ogan nasu. Kai tsaye TJ ya amsa masa da, ā€œAlhaji yana cikiā€.
          ā€œOkay to bari na gansa ko?ā€.
       Da girmamawa suka amsa masa da to. Shi kuma yay gaba kai tsaye sashen bedrooms ɗin Maash, suma sai suka fice dama abubuwan da suka dawo da shi a mota suka shigo da su ciki. A bedroom ɗin da yafi ʙyautata zaton samunsa yay knocking. Kusan mintuna biyu aka buɗe ʙofar. Ɗan zuba masa idanu Maash dake ɗaure da towel jikinsa na raɓar ruwa alamar daga wanka ya fito yayi. Sai kuma ya ɗauke kansa fuskarsa na sake zama kicin-kicin. Batare da ya ce komai ba ya saki ʙofar ya juya ciki. Bin bayansa Paah ɗin yay shima, a bakin katafaren gadonsa ya zauna, yayinda shi kuma yake daga ɗan lungun closet ɗin sa yana ʙoʙarin zira jallaniya fara tass mai gajeren hannu. Fuskarsa a tsananin ɗaure ya sake fitowa. Batare daya kalli Paah ɗin ba ya jingina da mirror daga tsaye yana kallon wani gefen. Kaɗan ya motsa lips ɗinsa wajen faɗin, ā€œGood Eveningā€.
    Karan farko Paah ya saki murmushin ʙarfin hali, sai kuma ya amsa da, ā€œEvening dear, how are you?ā€.
    Shiru Maash bai amsa masa ba. Sai ma ʙara ɗauke kansa da yay gefe. Shiru ɗakin shima Paah bai sake magana ba yana ʙulla ta inda zai fara. Kafin ya nisa a hankali ya sake furta. ā€œMuhammad magana nazo muyiā€.
               ā€œIna jinkaā€.
         Ya amsa masa a daʙile. Kai kawai Paah ya girgiza. Sai kuma ya cigaba da faɗin, ā€œKana fushi da ni ko? Akan abinda kaji ina faɗa. Haba Muhammad, kafa san yanda nake ʙaunar Ummu-Hidaya. Taya zan iya wofantar da ita saboda ta samu laluraā€.
            ā€œPaah ka faɗi abinda ya kawoka kai tsaye Pleaseā€. Maash ya katsesa cikin zafin raiā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’˜š’†š’š’—š’†

    ……Zuru Paah yay masa yana kallo, sai kuma ya haɗiye yawu masu kauri yana jinjina kansa. ā€œMuhammad wai sai yaushe zaka yarda dani akan mahaifiyarka ne? ʘarshen maganata da kawai kaji baka san akan mi nakeyi ba, ba kuma kasan dawa nake yi baā€.
          Fuska sosai Maash ya yamutse ransa na ʙara masa suya akan halin mahaifin nasa. Duk yanda yaso danne kar ya biye masa bazai iya ba, a fusace ya bashi amsa da, ā€œSai randa ka canja Paah. Sai randa ka ajiye son zuciya ka tuna da halacci. Bazan hanaka yin dukkan abinda kai niyya ba. Sai dai wlhy ina gab da ɗaukar mummunan mataki. Sannan yaronka na bashi nan da kwana uku ya sallami waɗan nan Ę“an iskan yaran daya tara min a company, idan ba hakaba duk wani mai alaʙa dasu ya kuka da kansa. Kuma shima ya ajiye aiki da hannunsa kar ya bari na ziyarci Company yana cikiā€
          Cikin ɓacin rai da tsarguwa Paah ya ce, ā€œMuhammad kana zargina ne?ā€.
          Shiru yay yaʙi tankawa. Sai da Paah ya miʙe zuwa gabansa. Cikin sauke murya ya sake furta, ā€œMuhammad miyyasa kai baka yafiya ne? Miyyasa kake da riʙo? Sai yaushe zaka yarda dani? Dan kawai kaji ina waya sai ka fasaarata da wata siga daban har kana tunanin sallamar waɗanda basu ji ba basu gani ba daga aikiā€.
                ā€œSai randa ka daina saka wannan ɗan iskan yaron na maka kawalcin yara ana kawosu da sunan wai ma’aikata. Paah na sanka fiye da yanda nasan kaina. Dama na jima ina zargin waɗan nan yaran zaman iskanci suke min a company. To wlhy na basu daga daren yau zuwa gobe su koma inda suka fito, in ma gidan karuwai zaka buɗe musu bai shafeni ba rayuwarka ceā€.
          Rumtse idanu Paah yayi da ʙarfi. Sosai kalaman ɗan nasa ke masa amsa kuwwa a cikin kunne. Yasan wanene Awwab idan yay fushi. Sam baya tauna magana yayin faɗarta balle shakka. Jin alamar zai bar wajen ya sashi buɗe idanunsa. Cikin ɓacin rai ya dakatar da shi da faɗin, ā€œMiyasa baka tauna magana yayin furtata? Ina matsayin mahaifinka amma baka shakkar tauna magana yayin furta min ita. Komai ya zo maka a rai saika yaɓosa wajeā€
               A daʙile da yanayin zafin rai shima Maash ya furta, ā€œNi ɗankane bani da hurimin hanaka duk abinda ka tsarama rayuwarka kam. Amma ka sani bazan iya cigaba da jurar ganin kana kana takamin mahaifiya a ʙarʙashin takalman ʙafarka ba Paah. Abinda na ɗauka kafin yanzu bazan iya ɗaukarsaba a yanzu. Idan da kace rashin mace ke saka aikata abinda kake aikatawa yanzu minene hujjarka kuma tunda kana da wata matar? Kai da kanka kamin alʙawarin dainawa, ashe baka fasa ɗin ba. Idan mace ɗaya ta maka kaɗan ka ʙara auren mana. Ka ʙaro uku su zama huɗu yafi min wannan mummunar ɗabi’ar taka mai zubar da mutunci ga zunubi wajen UBANGIJI…..ā€ ya ʙare maganar cikin ʙaraji dasa hannu ya watso kayan saman mirror ɗinsa gaba ɗaya. Sai kuma ya kaima mirror ɗin naushi, a take kuwa ya shiga tsatstsagewa. Sake kai masa wani naushin yayi, ya kuma tsagewa tare da jimasa ciwo. Sai ga saman yatsunsa duk jini ya ɓata. Da sauri Paah ya kamo hannun nasa jikinsa har rawa yake. Amma Maash ɗin sai ʙoʙarin ʙwacewa yake yi. Dan so yake kawai ya ʙara kaima mirror ɗin duka ko zai samu sauʙin zugin da zuciyarsa ke masa…
               ā€œPlease sweetheart relax. Dan ALLAH try to calm down. Jifa yanda kake jima kanka ciwo Muhammadā€.
          ā€œIs not your business Paah. I beg you leave me aloneā€.
        ā€œNaʙi ɗin, nace maʙi na barkan! Miyasa kake da zuciya ne Muhammad. Fushinka yayi yawa. Taya zan Barka ka cigaba da jima kanka ciwo. Nace kayi haʙuri! Haba Muhammadā€. Ya ʙare maganar cikin sanyin murya tare da jawoshi jikinsa ya rungume. Abinka da su duka dogaye, sai gasu kai ɗaya. ʘarfi da cikar zati kawai Maash zai nuna masa saboda shi yana akan ʙuruciyarsa, shiko koba komai girma ya kamashi.
           Luff Maash yayi a jikin mahaifin nasa, sai faman sauke zafafan ajiyar zuciya yake a jajjere. Yayinda Paah ke jin yanda zuciyar tasa ke gudu da ʙarfi. Sunfi mintuna uku a haka sannan ya ɗagosa. Kama hannun nasa yay suka nufi wajen gadon, zaunar dashi yay sannan yaje ya ɗakko first aid box ya dawo kusa da shi ya zauna. Hannun nasa dake ta tsatstsafo da jini ya kamo, cike da kulawa ya fara masa treating. Ko sau ɗaya Maash bai motsa ba, bai kuma kalla mahaifin nashi ba har ya kammala ya naɗe masa da bandage. Zama yay zai fara magana Maash ɗin kawai ya miʙe, da sauri Paah ya riʙosa ya maida shi ya zaunar. Bai musa ba ya zauna, sai dai yaʙi kallonsa yanzu ma. Shiru Paah yay yana kallonsa, sai kuma ya sauke numfashi a hankali yana sake tattaro abinda yake son faɗar. ā€œMuhammad kayi haʙuri, tabbas nasan bana ʙyauta muku, sannan ban yima kaina adalci ba. Bazan kira abinda nake aikatawa da ʙaddara kawai ba, harda sa kai. Shiyyasa tabbas a rayuwa ka guji aikata mummunan aiki a ʙuruciya, idan kuma ya zama jarabawarka ce ka fara kayi gaggawar tuba. Idan ba haka ba wannan abin zai ta bibiyarka ne a lokacin girma, a lokacin da kuma kake son ka daina ɗin amma abin yabi jininka. Wannan maganar mahaifiyarka tasha faɗa min ita da maimaita min a duk sanda ta sameni a halin rashin gaskiya. Amma mi a lokacin bana gane karatunta, gani nake ai duk sanda na shirya zan iya dainawaā€. Yay murmushin takaici, mai nuna ainahin ciwon da yake ji a zuciyar yasa. Cikin ɗan yarfar da hannu ya cigaba da faɗin, ā€œAbubuwa da yawa sun faru, wasu ma suna kan faruwa da ni kaina ban san adadi ba. Ni ne ya kamata ace na tsaya muku, amma sam ban taɓa yunʙurin hakan ba koda sau ɗaya. Hatta da rashin Fahad a kusa da mu yana damuna. Sai dai ban san taya zance komai ba. Muhammad! Banso ace halin da nake ciki yayi nason da zai shafeku ba kamar yanda mahaifiyarku tasha yin fata. Sai dai a wannan gaɓar na fahimci zancen nan na masu iya magana da kance TSUTSAR NAMA ITAMA NAMA CE. Wlhy bazan ɓoye maka ba, case ɗinka akan yarinyar nan ya tsaya min ta yanda na kasa haɗiyeshi, sannan yanda kake bama yarinyar kulawa tamkar ba abinda ake gudu bane ya shiga tsakaninku na sake ɗaga min hankali. Bana son ace sunanka ya ɓaci a duniya Muhammad, wlhy bana son abinda wani zai aibantaka da shi, koda bazan ce komai ba ina jin zafi, matuʙar zafi a cikin zuciyata. Dan ALLAH ina roʙonka idan an sallami yarinyar nan daga asibiti gobe idan ALLAH ya kaimu zan haɗa mata sha-tara ta arziʙi tare da siya mata ticket ɗin jirgi idan ba Ę“ar cikin garin nan bace ta koma garinsu. Idan kuma a cikin garin nan take da iyayenta nasan zata iya yiwuwa a gidan haya suke ko wani muhalli ʙaskantacce. Zan saya musu gida a ɗaya daga cikin jihohin arewa su koma can, kar su sake waiwayar Lagos har abad….ā€
          Karan farko Maash ya zuba masa idanun kawai yana masa wani irin kallo mai wahalar fassara. Kallon ne ya dinga ratsa Paah sai ya gagara ʙarasa abinda ya faro ya ja bakinsa kawai yayi shiru. Wani irin murmushin ʙasaita da ɓacin rai Maash yayi, sai kuma ya ce, ā€œYa kayi shiru kuma, ina jinka Paah.ā€
              ā€œSaurarena kawai kake amma ba jina ba Muhammad abar maganar kawaiā€. Ya faɗa cikin ɗan borin kunya da kame-kame. ā€œKa kwanta ka huta dare yayi, zuwa safiya sai mu ʙarasa, amma ka daina kira min ʙara aure har ma na mata uku, kai ka sakar min Ummu-Hidaya ɗin ne da kake cireta a matsayin matataā€. Ya sake faɗa yana nufar ʙofa cikin Ę“ar sassarfa ya fice. Tsahon lokaci Maash ya ɗauka yana kallon ʙofar kawai. Sai kuma ya cije lips ɗinsa da masifar ʙarfi zuciyarsa na masa wani irin suya. Yasan mahaifinsa fiye da sanin da kowa ya masa a rayuwa. Amma bazai ce komai ba ALLAH mai ji ne mai gani. Yana kuma roʙonsa ya shiryeshi…

          🤄Humm, kai dai Paah ALLAH ya shiryeka dai to gaskiyašŸ˜. Yayanmu kayi haʙuri mahaifi mahaifine koda na banza ne😭.
        
           šŸ’¦āœØšŸ’¦āœØšŸ’¦

         Tun wucewarsa daga asibitin abubuwa suka sake cinkushe min kai. Kalamansa sai faman maimaita kansu suke a cikin kaina. Duk da nasha magani zafin zazzaɓin nan yaʙi bari na. Zaune na tashi ina kallon Mama Balki da barci ya ɗan fara figa. Sai kuma na miʙe cikin sanɗa na nufi ʙofar fita.
             ā€œSamraah ina zaki je?ā€.
         Muryar Mama Balki a bazata ta daki cikin kunnena. Cak na tsaya tare da runtse idanuna. Sai kuma na juyo a hankali cikin son wayancewa zanyi magana ta dakatar da ni.
    ā€œBaki iya ʙarya ba Samraah, kada ki farata yanzuā€.
       Sosai furucin nata ya dakeni, dan haka na sauke ajiyar zuciya tare da dawowa a hankali na koma saman gadon na zauna. Kaina a ʙasa ina wasa da yatsun hanuna nace, ā€œKiyi haʙuri Mama. Ba wani abu zanyi ba. Reception zanje na samo pen da takarda zanyi amfani da suā€.
                ā€œAmma a daren nan Samraah. Na kula tunda Alhaji ʙarami ya tafi baki da nutsuwa. Bana fatan ace kina son samo takarda da biron ne dan kiyi rubutun da zaki bar masa ki guduā€.
        A karo na farko nayi murmushi tare da girgiza mata kaina. ā€œHaba Mama, ai a yanzu wlhy koda shine da kansa yace na tafi gidanmu bazan je ba. Dan insha ALLAHU sai na sauke alkawarin dana ɗauka akan Ummie. Kawai zanyi amfani da sune dan ina son yin lissafi dalla-dalla. Ba kuma zai yiwu a cikin ʙwaʙwalwa ba dole sai da taswira a rubuceā€.
         Ajiyar zuciya Mama ta sauke. Batare da tambayata abinda zanyin ba ta miʙe. ā€œShike nan ki zauna ni bari na fita na samo miki. Kin san dai ba’a son ki yawaita motse-motse mai ʙarfi saboda ɗinkin jikinkiā€.
          Bance mata komai ba sai duʙar da kaina dana sake yi. Itama sai ta fice abinta bayan ta zumbula Hijjab ɗin ta……….āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’‰š’Šš’“š’•š’†š’†š’

    ……Mintuna basu fi biyar ba kuwa sai gata ta dawo. Cike da farin ciki ta miʙa min takarda da biron tana faɗin ā€œKinga Alhamdullah na samu Ę“ar arziʙi a reception ɗin ma. Ina tambaya babu musu ta ciro ta bani har shida, gasu kuma manya nasan dai zasu isheki ai ko?ā€.
             Nima fuskata a washe da murmushi na amsa ina faɗin, ā€œYauma Mama Nagode sosai. In sha ALLAHU zasuyi harma ʙila suyi yawa.ā€
       File ɗina na ɗauka na ɗaura a samansu tare da gyara pen ɗin. Gaba ɗaya ahalin Maash Mansion na shiga lissafowa a jere. Wanda na manta ina tambayarta. Hatta da adadin masu aiki maza da mata da aikin kowa sai da na rubuta su. Kafin nabi duk manyan gidan na zana halin kowa dana fahimta agaban sunansa. Hatta shi kansa Maash ɗin harda shi. Daga haka nai shiru ina nazari tsahon lokaci, kafin na ɗaga katifar na saka takardar. Toilet na nufa na ɗauro alwala. Duk da yanda nake jin jikina haka na nutsu na kabbara salla domin miʙama UBANGIJINA kukana tare da kai ʙarar wasu mutane garesa dan ya shigemin gaba wajen gano ainahinsu kozan san inda zan kama a wannan tafiyar dana shirya yi….

       šŸŒæšŸ’žšŸŒæšŸ’žšŸŒæ

             Sosai biki ya kankama a gidan Abba Imamu. Sai dai gaba ɗaya bai zoma Mom a yanda ta shirya shi ba. Dan har yanzu Abba yaʙi maidata ɗakinta. Babu irin haʙurin da bata bashi ba, hakama Ummanta tazo ta saka wanda yake jin kunya amma yaʙi sauraren kowa. Kasancewar tana a cikin gidan har yanzu yasa mutane da yawa basu san abinda ke faruwa ba. Abun zai baku mamaki idan nace muku tunda Halime ta fuskanci abinda ya faru tsakanin Mom da Abban itama ya kasa gane kanta. Kuka ta dinga masa da magiya da roʙon ya maida matarsa, idan ba hakaba itama gaskiya sai dai ya saketa. Ita haka kawai yaja mutane su tsaneta a dinga cewa dan ya aurota ne ya saki uwar Ę“aĘ“ansa. Duk yanda ya nuna mata babu ruwanta a ciki taʙi haʙura ta barsa. Kullum cikin masa nagiya take da kuka gashi bata da lafiya sosai. Dan ta kai ma a yau sai da suka je asibiti saboda yanda take amai gaba ɗaya ta galabaita. An tabbatar musu tana da shigar ciki. Zo kuga murna wajen Abba. Yayinda Halime ido yay gwalo-gwalo. Tabbas tana son yara sosai, kodan yanayin rayuwar data gashi ta tsangwama da rashin sakewa. Bata da wani wanda zatace yau ya zame mata amini tunda ʙaninta ya rasu. Ba kunya Abba na dawowa gida ya barbaɗama Auta. Murna da tsalle Auta ya dinga yi da ga ʙarshe ya kwasa da gudu yaje ya barbaɗama Mom dake tare da ʙanwarta da Ummanta da suketa tsare-tsaren biki da za’a fara nan da kwanaki biyu. Neman ɗaukewa numfashin Mom ya yi, har sai da takai hannu ta dafe goshinta dan wani irin sara mata kanta yayi na masifa. Ganin tana neman ɗagama kanta hankali Ummanta da ʙanwarta suka shiga lallashinta da mata nasiha akan tafa kwantar da hankalinta. Wata fitina ko nuna wani abu a yanzu ba nata bane. Ita da ake lallaɓawa ya maidata ɗakinta ya kamata ace ta nutsu, kai kodan bikin nan da za’a tara mutane ta rufama kanta asiri karta bari Ę“an uwansa su samu lagonta. Dan yanda bata riʙesu hannu biyu ba sumafa a yanzu dole su ringa nuna mata cewar amarya ta fita a wajensu. Sannan duk hanyar da zasu ʙuntata mata a shirye suke da nemota komai ʙanʙantarta. Shi kansa Abban yanda yake jin kansa on top akan yarinyar nan yanzu idan fa ta cigaba da matsawa sauran igiya biyun ya tsinketa ba abinda zai damesa bane.
           Wannan nasiha da ʙanwarta ta mata ne ya sakata kama kanta badan taso ba. A haka aka shiga shagalin bikin Baby. Danginta da Ę“an gwarzo sun cika gida tako ina. Tun ranar alhamis aka fara event, dan wasu irin mahaukatan kuɗaɗe mijin Babyn ke kashewa tamkar baisan ciwonsu ba. Duk da kuwa bikin Abba ya dawo dashi baya ne akan yanda aka sanyashi an zaftare har sati biyu a ciki. Ranar juma’a aka kawo lefe na nunama tsara harda key ɗin motar da aka zubo kayan. Wannan bajinta ta ragema Mom raɗaɗin dake damunta a cikin zuciya game da cikin Halime. Ta dinga yanka ʙananun habaici da ɗagawa ma mutanen Gwarzo. Faɗa take yanzu ne akai biki na Ę“ar gata ba irin na Samraah da har yanzu basu san ina ya dosa ba. Maybe ma Abba da Musaddiq sun saidata ne ko turata karuwanci. Yo inba haka ba wane irin aurene wata kusan takwas basu taɓa sanin miji ba itama bata taɓa zuwa gida ba. Ai dole ne akwai abin ashshar da ake ɓoye wa. Duk da kalamanta sun tada hankulan su Gwaggo Gudidi duk da zuwa yanzu suna waya da Samraah dan hatta su Kawu Musa tana ɗan kira sai suma suka ji kamar basu ʙyautama Samraah ɗin ba. Amma dai sun shanye a fuskokinsu babu wanda ya tanka Mom da haukarta. Washe gari asabar aka ɗaura aure. Abu na farko daya fara bama mutane mamaki shine ango daga shi sai abokansa guda uku yazo wajen ɗaurin auren. Sune suka amsa masa auren a matsayin waliyyay. Kowa yayi zato da tsammanin yanda yake faman ɓarin kuɗi kamar babu gobe sai ʙofar gidan Abba an rasa wajen faka motocin gayyarsa data ango. Amma sai gasu su huɗu a mota ɗaya rak kamar dangin mayu. Jikin Abba shi kansa ya fara sanyi, sai dai bai iya yace komai ba har aka kammala. Zuwa dare maimakon an shirya amarya a miʙata ɗakinta sai akacema Abba wai ai wajen dinner za’aje sai zuwa gobe ango zai ɗauki amaryarsa daga gidansu sai airport zasuje honeymoon ne. Sai bayan sun dawo zai wuce da ita gidanta. Tofa anan ne fa ʙananun magana suka ɗan fara tashi, haka aka shirya tafiya dinner kowa bakinsa da abin faɗa. A wajen dinner an ɗan ga wasu mata a matsayin danginsa. Sai abokansa da suka ɗan zazzo da matansu. Dan ko wajen bada tarihinsa ʙanwarsa ce ta bada. Dinner kam tayi dinner, dan anci kaji ansha lemon roba gwargwadon iko. Ga bag da aka raba cike da kayan rabo a ciki. Amarya baby da ʙawayenta sai feleʙe ake abin nema ya samu. Haka Mom dan tare da ita akaje dinner sai nuna isa ake. Hatta da Umma sai da taje abinta ko kunya. ʘarfe ɗaya da wani abu na dare aka tashi, su dai Ę“an Gwarzo ma tun kusan goma da wani abu suka saka Musaddiq ya dinga fito da su yana sakawa a napep ana maidosu gida dan sun gaji. Lokacin da su Mom suka dawo su tuni sunyi nisa a barci. Ita kam Halime dama bata da wani sakewa a bikin saboda laulayinta mai addaba ne. Koda yaushe tana ɗaki kwance. Da ʙyar take ɗan yin dauriyar fitowa ta gaida Ę“an gwarzo. Dan hakama dinner ɗin bataje ba sukai zamansu ita da Abba a gida yana tattalin kayarsa da lallashi itako tana zuba masa taɓara..
          Washe gari lahadi da aka tashi da shirin wucewar baby da mijinta shi kuma Musaddiq ya shirya wutowa Lagos. Sunyi waya da mijin Samraah zai je wajenta ya kwana washe gari litinin zai haɗu da wanda zai masa jagorar wucewa ʙasar Chaina kamar yanda MD ɗin sa ya bashi a rubuce. Dan haka ya shiga sallama da Ę“an uwa anata koke-koke. Abinka da tsoffi gani suke tafiya Chaina ɗin nan kamar tafiya lahira ne. Dan wasu ma da farko da ca sukai basu yarda Musaddiq ɗin yaje ba. Sai da Abba ya dinga basu haʙuri da nuna musu muhimmanci da cigaban da Musaddiq ɗin ya samu har suna wataran zai shafesu sannan suka haʙura badan sun so ba. Sai dai sunyi farin ciki da jin shi da Hafizzullah zasu je wajen Samraah ne a yau kafin shi ya wuce gobe. Dan rigima da Hafizzullah ya saka masa akan son zuwa shima yaga Samraah ɗin ne yasa shi fidda yan kudaɗensa ya saya masa ticket ɗin jirgi saboda shi ta sama zaibi zuwa Lagos ɗin sai ya saima Hafizzullah ɗin shima zasu wuce tare. Kafin ma mijin Baby ya iso su sun fito, dan motar company ce zata kai Musaddiq ɗin airport. Haka suka wuce Ę“an uwa da abokan arziʙi na musu fatan alheri. Tare da saʙon gaisuwa ga Samraah buhu-buhu aunty Zakiyya harda saʙo a cikin kwali datai nannaɗe da su Musaddiq basu sani ba. Hakama Gwaggo Gudidi ta haɗa kayan maʙulashe irinsu tuwon madara, carbin malam, gullisuwa, aya, gyaɗa, riɗi, cike da leda viva tace a kaima ɗiyarta. Wai maybe tanada ciki kunya ta hanata faɗa, ba kuma a raba masu ciki da son kaya kwaɗayi irin waɗan nan. ALLAH sarki Halime itama sai da ta bada zuma mai yawa a gora da uban aya da take saidawa a kaima Samraahn duk da a hoto kawai ta santa. Ta kuma saka Abba dole ya bada naira dubu hamsin a kaima Samraah ɗin. Sosai Musaddiq yayi mamaki bada waɗan nan kuɗi, amma haka kawai sai yaji a ransa aikin aunty amarya ne. Sosai yaji kima da darajar yarinyar na ʙaruwar masa a rai, har sai da ya share ʙwalla. Dan tunda tazo gidan nan abubuwa da yawa suka sauya. Abincinsa, tsaftar ɗakinsa bata ʙyashin shiga ta gyara, komai kuma tana yimasa a mutunce da girmamawa. Yana kiranta aunty tana kiransa Yaya. Da yay magana sai tace ai ita ɗan uwa take kallonsa kuma babban yaya bawai ɗan mijinta ba. A bata da lafiyar nan duk rintsi bata bari ya fita da safe bai karya ba koda ba ranar girkinta bane. Haka tunda Hafizzullah yazo take hidima da shi da jansa a jiki shima kai kace ʙaninta ne uwa ɗaya uba ɗaya. Duk yanda Hafizzullah keda ʙin sakin jiki da mutane sai gashi dandanan ya saki jiki da ita. Hatta da jakar kayansa yanzu haka a ɗakinta ya bari dan ɗakin Musaddiq ɗin akwai baʙi maza yan gwarzo da basu kai ga wucewa baā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’‡š’š’“š’•š’†š’†š’

    ……Lokacin da suka iso airport ɗin su duka sai da ʙwalla ya cika musu idanu. Dan abune da basu taɓa zato ko tsammani ba a rayuwarsu. Sune yau da hawa jirgi daga Kano zuwa Lagos. UBANGIJI al-musawirru mai sassauya al’amura a sanda yaso ga kuma wanda yaso. Da suka shiga jirgin sai Hafizzullah ya rungume yayan nasa yana hawaye. Dole shi ya haɗiye nasa ya dinga lallashinsa. Bayan yayi shiru kuma ya dinga musu video wai dolene ya nunama Aunty Samraah yau sun hau jirgi. Dariya Musaddiq ya dinga masa har ALLAH ya saukesu lafiya garin Lagos. Sunyi mamakin ganin zuʙeʙiyar motar da tazo ɗaukarsu. Amma sai Musaddiq bai kawo komai a ransa ba tuna cewa dafa companyn Maash yake aiki, mai lamba ta ɗaya a Africa, na uku a duniya a matasa. Ai hakan ba komai bane ba. Sunyi da MD dama motar company zata daukesu daga airport ta kaisu duk inda zai je, sannan idan ya kammala gobe idan ALLAH ya kaimu zai kira aje can gidan Ę“ar uwar tasa a ɗaukesa zuwa wajen GM, daga nan zai wuce kuma….

    🩸🩸🩸🩸🩸

           Kamar kullum alarm ɗinsa ne ya tashesa. Hannu ya kai idanunsa a rufe ya lalubosa a saman side drawer ya danne wajen kashewar dan shifa ko yaya ʙara take damun rayuwarsa take. Shiyyasa bazaka taɓa ganin wayarsa da ringing ton ba. Kullum cikin vibration phones ɗinsa suke. Hakama television da wahala kiji ya buɗeta caaa tana surutu. Cikin mayen barcin da bai gama isarsa ba ya nufi toilet. Sai da yay wanka kamar yanda abun ke neman zame masa sabo saboda mafarki duk da ba kullum yake tashi a irin yanayin ba sannan ya ɗauro alwala ya fito. A ɗan gurguje ya busar da kansa ya shimfida sallaya yay raka’atainul fijir sannan ya fice masallaci. Ana idar da salla bai yarda sun haɗu da Paah ko Uncle Abdullahi ba ya dawo gidan. Jallabiyarsa ya zare ya ɗauka sports wear ya saka masu kalar blue da rashin white. Sosai kayan sukai masa ʙyau duk da baya sakasu ne domin kwalliya ba. Ya kama gashinsa ya haɗe a tsakkiya tare da ɗauresa da siririn baʙin band. Duk da gudu zai fita sai da ya sakama jikinsa turare ya maʙala bluetooth a kunensa sannan yay zaman saka takalma spots na companyn nike. Yana fitowa falo Laalah dake kwance ya miʙe ya nufosa. Kansa ya shafa cikin lumshe idanu da silent voice ɗin nan tasa ya furta, ā€œLet’s go my friendā€. Cikin kaɗa bindi kuwa ya bisa abin cike da mamaki. Daka gansu kasan karen ya gama samun training na musamman a hannun uban gidan nashi. Gashi fari tass babu alamar wani dattin ʙazanta a tare da shi. Wanda ma bai sani ba sai ya ɗauka ba kare bane saboda yanda jikinsa ke duguzum da gashi. Yana nufar gate da ɗan gudu Laalah biye da shi ʙafa da ʙafa dan a jere suke tafiya su Sha’aibu dake zaman jiran fitowarsa na take musu baya suka fice yana ɗagama ma’aikatan daketa faman gaishesa hannu. Gudun ya fara tun daga wajen gate ɗin a hankali Laalah a gefensa guards ɗinsa biye da su. Haka suka miʙe street ɗin nan. Sosai sukayi nisa bana wasa ba. Jefi-jefi suna gamuwa da mutane da suma suka fito jogging ɗin. Hannu kawai suke ɗagama juna kowa ya wuce. Sai wasu Ę“ammata ne da suka dai-daita gudun kusan da shi dan suna a ɗan gabansa kaɗan amma ko kallo basu ishesa ba. Sunyi nisa sosai ya jiʙe sharkaf da zufa har yana ɗiga sannan suka sake juyowa bayan ya kalla agogon dake a tsintsiyar hannunsa. Suna isowa kwanar da zata sadasu da gida ya tsaya cak. Nuni yayima Shu’aibu daya bashi ruwa cikin sauke numfashi da sauri-sauri. Da sauri ya nufesa tare da ajiye Ę“ar jakar da abubuwan da zai buʙata ke’a ciki. Kamar su bottle water, towel da abinda ba’a rasa ba. Ruwan ya amsa ya buɗe murfin haɗaɗɗiyar bottle water ɗin ya kai bakinsa. Kansa ya ɗaga sama ya shiga kwararawa. Wani irin kaiwa da komawa maʙoshinsa ya shiga yi, illahirin ʙofifin gashin jikinsa na buɗewa zufa na fitowa da gudu. Sai da ya sha fin rabi sannan ya sauke gorar yana sauke numfarfashi. Laalah ya zubama kaɗan a jiki, shiko yay wani irin matsawa yana girgiza jiki. Yanda yay ɗin ne ya saka Maash ɗin sakin wani ɗan guntun murmushi yana sake kai goran bakinsa ya ɗan kurɓa sannan ya rufe ta ya miʙama Shu’aibu da suma duk suke shan nasu ruwan tare da masa alamar ya bashi towel. Da sauri ya miʙa masa fari tass ɗin towel ɗin hannunsa dake a linke. Sai da ya fara gogo wuyarsa zuwa gashi dake kwance a kumatunsa sannan yay magana batare da ya kalli su Shu’aibu ba.
          ā€œKira Tijjani ya samemu anan da motaā€.
          Duk da a hankali yay maganar sarai Shu’aibu ya jisan. Sai dai yayi mamakin jin abinda yace ɗin. Amma bashi da hurumin musawa. Sai ma waya daya zaro yay kiran TJ ɗin. Cikin ʙanʙanin lokaci motocin biyu suka iso. Ta farkon aka buɗe masa ya shiga shi da Laalah. Ta bayan guards ɗinsa ne. Sai TJ da Shu’aibu a gaba tunda ba Hayatu. A ɗan ɗarare TJ ya ce, ā€œSir ina zamu je?ā€.
         Shiru kamar bazai ce komai ba. Sai kuma can a ʙasan maʙoshi ya furta, ā€œHospitalā€.
          Da girmamawa TJ ya amsa da, ā€œAn gama ranka ya daɗeā€ yana tada motar. Kansa kawai ya kwantar jikin kujera ya kumshe ido. Har lokacin zufa na faman tsatstsafo masa. Bai ɗago ba har sai da suka isa asibitin. Shu’aibu ya buɗe masa da sauri ya fito. Sai dai banda Laalah shi an barsa a motar. Cikin takun nan nasa ya nufi cikin asibitin Shu’aibu da TJ biye da shi. Tako ina tsirarun ma’aikatan cleaners da ma Nurses da sauransu sai kalonsu suke. Koda suka shiga reception tuni yammatan dake a kan katan sun miʙe bakunansu a washe suna masu Barka da zuwa idanunsu a kansu kamar tsoffin mayu. Ko kallo basu ishesa ba sai su TJ suka amsa musu…
      
             Kuka na gama zabgama mama Balki akan nifa yau ko su sallamen daga asibitin nan kona gudu gida. Dan bazan sake kwana banje naga halin da Ummie ke a ciki ba. Lallashina taitayi akan nayi haʙuri jikina ya ʙara ʙyau tunda doctor tace sai nan da kwana biyu, jikin Ummie kuma da sauʙi sosai. Tirjewa nayi akan nifa sai na tafi. Ganin yanda nake zabga uban kuka yasa Maman cewa shike nan naje nayi wanka idan Alhaji ʘarami yazo anjima itama zata sake masa magana da kanta. Badan naso ba nabi umarninta. Kamar kullum sai da ta fara taimaka min na shiga ruwan zafi na mintuna goma sha biyar zuwa ashirin da nake yi sau uku a rana. Sannan ta fito akan nayi wankan bara taje ta dawo.
          Wankan na ʙarasa batare da tunanin kowa zai iya shigowa ba na fito ɗaure da towel kawai. Dan masu shara tun sanda zan shiga cikin ruwa Mama Balki ke cemin sun shigo aikinsu. Haka dama sukeyi, kullum tunda sassafe zaki gansu, wani lokacin ma ana idar da sallar asuba. Daga nan kuma sai da rana, sai kuma yamma. Fes kuwa na samu ɗakin harda turaren wuta sun kunna. Jikina na goge da ɗan hanzari. Bana son Mama Balki ta shigo ban saka kaya ba duk da nasan ko tazo ɗin tsayawa take bakin ʙofa sai ta tambayi na shirya sannan ta shigo, dan kunyarta nake ji matuʙa. Ƴar jakar kayanmu na buɗe na ciro b&p da zan saka dan ni ina amfani da kayan asibitin ne. Bra ɗin na fara ʙoʙarin sakawa da sauri-sauri, na saka hannu ɗaya ina ʙoʙarin saka ɗayan kawai ya zaro ta baya. Fuska na ɓata kamar zan fasa kuka, abinda dai nake gudun sai ya faru, tunda dole na jira Mama Balki tazo ta maʙala min ko kuma na cire na sake sakawa tazo ta sameni, amma bari muga na gwada dai kozan iya nawa ʙoʙarin. Kicin-kicin maidawa na fara ina famar cizar lips, sai kawai naji saukar lallausan hannu mai bala’in sanyi akan nawa dake riʙe da hannun bra ɗin. Tabbas wannan ba mama Balki bace, dan wani irin mayataccen ʙamshi ne ya shiga ratsa ʙofofin hancina. A birkice na juyo gaba ɗaya na nama manta da wani batun saurin da nakeyi. Saukar idanuna cikin lulu cat ɗin nashi ya sani ja baya jikina har tsuma yake. Shiko ko gezau, sai ma wani irin kallon ʙurilla yake bina da shi idanunsa a shanye. Inda naga ya kafama idanun nima na kalla da sauri, ai da sauri na naɗe hannayena a wajen ina tura baki kamar zan fasa kuka. Kafaɗa ya ɗan ɗage tare da taɓe baki irin shi baiga abin kallo ba, ina ʙoʙarin sake juya masa baya sai kawai ya shiga takowa a hankali. Baya na sake jan jikina yana cigaba da biyoni duk na ruɗe. Jin na dangane da abu yasa na juya da sauri na kalla, sai naga bangone, tashin hankali anzo the end kenan inji bature. Banda zaɓin daya wuce kawai na juya masa baya na kalla bangon. Idanuna a runtse murya na rawa na ce, ā€œWai da ALLAH minene haka kake yi? Ni dai ka fita kayafa zan saka, sai Mama ta shigo ta gankaā€.
         Maimakon amsa min ko ya fitan sai kawai naji ya saukar hannunsa akan kafaɗata, da ʙarfi na sake matse idanun nawa jin yanda yake wani irin tafiya da yatsun kamar mai yi da gayya……..āœļø

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’‡š’Šš’‡š’•š’†š’†š’

    …Hannun bra ɗin ya maʙala min a inda ya zare, a tunanina zai matsa ne sai naji saɓanin hakan. Matsoni ya sake yi ta yanda har nake jin saukar numfashinsa a saman wuyana, sai kuma ya saʙalo hannun nasa ɗaya ta saman cikina. Yanda na sake matsewa a bangon bai hanashi jawoni baya ba a hankali, kansa ya ɗoro a saman kafaɗata tattausan gashin kumatunsa dake da laimar da nake ʙyautata zaton zufa ce tunda sports wear ne a jikinsa na gugar gefen fuskata. Ɗayan hannun ya ɗaura a saman nawa dake rufe da ʙirjina har yanzu zai zame, aiko naʙi yarda na sake ʙanʙamewa.
           ā€œNa cire towel ɗin kenan?ā€.
        Soft voice ɗin sa dake fita low sosai cikin maʙoshi ta ratsa kunnuwana. Kaina na girgiza masa alamar a’a idanuna na cika da ʙwala.
        ā€œOya remove your hand kona ciresa tasā€.
        Nasan zai iya, dan kaɗan daga ʙaramin aikinsa ne. Dan haka na shiga zamesu a hankali hawayen da nake maʙalewa na sake taruwa cikin idanun. Sake matsesu nayi jin yanda yake jan towel ɗin a hankali, har ya gama sauke b ɗin kan jikina babu kunya babu tsoron ALLAH ya gyarata ta zauna da ʙyau sannan ya maida min towel ɗin a sama.
           ā€œI love white musamman yanda wannan ta miki ʙyauā€. Ya faɗa cikin kunnena cikin raɗa.
       Da sauri na toshe kunnena tare da ture masa kai dan bana ma son ji. Maimakon ya barni kamar yanda naso sai ma ya sake nanne ni da jikinsa tare da sumbatar wuyana da hannun dana toshe kunnen. Ni kaɗai nasan kalar masifaffiyar kunyar da nake a ciki da mamakin tasa rashin kunyar dan shi komai yana yinsa ne kansa tsaye. Mun kai tsahon mintuna biyu a haka sannan ya janye jikinsa a nawa tare da kama hannuna. Ban buɗe idanuna ba, sai alamar zaunar dani da naji yayi a bakin gado. Jin kamar ya jawo kujera ya zauna gab dani dan har ʙafafunmu na a cikin na juna ne ya sani buɗe idanuna dake mar-mar. Kamar yanda nayi hasashen hakanne kuwa. Ya jawo kujera gab da ni ya zauna hannunsa ɗauke da rigar asibitin da aka ajiye min a saman gadon. Idanunsa kan p ɗin dana ajiye. A zabure na kai hannu na ɗauke ina ɓata fuska kamar zan yi kuka na cikukuyesa a hannuna na tura ʙarʙashin cinyata. Mayatattun idanunsa ya zuba min tare da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, ā€œHandā€.
        Bani da zaɓin daya wuce miʙa masan kawai, dan nasan ko cewa nayi bana so bazai barni ba. Inaji ina gani ya saka min rigar sannan ya miʙar dani a gabansa kamar wata Ę“ar yarinya ya zare towel ɗin ya ajiye gefe. Hannu ya miʙa min wai na bashi p ɗin dana sake saurin ɗaukewa. Kafaɗa na maʙe masa ina juyar da kaina gefe. shima sai ya taɓe nasa bakin kawai. Turaren dana ajiye gefe ya ɗauka ya ɗan duba jikinsa, sai kuma ya ɗan sake taɓe baki kaɗan, batare da yace komai ba ya ɗan fesa min ya maida ya ajiye. Ni dai uffan bance masa ba, kaina a ʙasa ina wasa da yatsun hannuna. So nake na tambayesa yaya Ummie amma duk ya dabaibaye ni da salon da ban taɓa zaton gani daga garesa ba. Gashi duk abin nan da yake fuskar nan na’a tsukenta kamar bashi keyi ba. Da ʙyar na iya dauriyar faɗin, ā€œIna kwana? Yaya jikin Ummie?ā€.
          Jin shiru bai amsa ba ya sa na ɗago idanu na a hankali kamar wata matsoraciya. Kamar yanda nayi zato shima nasan a kaina suke, dan haka da gudu nai yunʙurin kauda nawa amma sai ya riʙo haɓata da yatsunsa biyu.
             ā€œIna miki aiki bazama kince kin gode baā€.
        Baki na tura masa. Cike da Ę“ar jarumtar dana tattaro a tsiwace nace, ā€œTo ni dai ai bance ina so baā€.
         Maimakon ya bani amsa sai naga ya saki wani shegen murmushi. Cike da suɓutar baki da mamaki na ce, ā€œLah yau ma kayi murmushiā€.
                Janye hannunsa yayi, tare da tsuke fuskar. Ni sai ma abin ya bani dariya. Sai kace wani ɗan yaro. Dariya nayi ina ʙoʙarin kare bakina na ce, ā€œIkon ALLAH, to kai baka so ace kayi murmushin ne? Sai kace wani abun mugun abu. ALLAH idan ma kayi murmushin kafi ʙyau. Amma kullum fuska a ɗaure kamar wani ma’aikin mutuwa.ā€ na ʙare maganar ina haurawa saman gadon gaba ɗaya tamkar banga irin kallon da yake faman bina da shi ba. Sai da naja bargon na rufe ʙafafuna sannan na kuma marairaice fuska. A hankali na ce, ā€œYaya Awwab!ā€. Shiru yaʙi amsa min, sake maimaita kiran sunan nashi nayi a shagwaɓe. ā€œYaya Please answer meā€.
          Nan ɗin ma kamar bazai amsa ba. Na sake ʙoʙarin yin maganar cikin harara ya katseni da faɗin, ā€œBa kunni ke ji ba neā€.
               Baki na tura sosai. Na ce, ā€œTo ai dai ba daɗi mutum yayi magana aʙi amsa masa.ā€
          Banza yay min bai tanka ba. Nima sai na cigaba da faɗin, ā€œDan ALLAH ka taimaka a sallaman yau a asibitin nan. Idan ba hakaba ALLAH zan gudo gida. Ina missing ɗin Ummie sosai. Ni wlhy na warke faā€.
                ā€œNa ganiā€.
           Ya faɗa kamar bashi ba yana ʙoʙarin yaye bargon dana rufama ʙafafun nawa. Da sauri na waro idanuna ina riʙe hannunsa. Kaji mun mutum to mizai gani?. Shanyayun idanunsa ya ɗago ya zuba min, ni kuma na marairaice fuska har idanuna na tara ʙwalla. Hannun ya janye kawai batare da yace min komai ba. Nima sai na sauke ajiyar zuciya dan al’amarin wannan mutumin yasha kan nawa ʙaramin tunanin gaskiya. Sake matsar da kujerar da yake zaune yayi gaban side drawer. Batare da yace komai ba ya shiga ʙoʙarin haɗa tea dan akwai babban basket mai murfi dake cike da kayan shayi kala-kala da su chocolate da kullum Hayatu baya gajiya da sayowa. Yo ni Hayatu ai zance tunda dai shine ke zuwa da su. Banda jiya da bai zo ba ɗayan yaron nan nasa da har yanzu ban san sunansa ba ya kawo snacks. Tea ɗin ya haɗa a zatona shine zai sha, har na fara gulmarsa a zuciyata sai naga ya miʙa min mug ɗin. Tsayawa nayi kawai ina binsa da kallon mamaki, dan haka muka ʙurama juna ido. Kusan minti ɗaya muna a haka kafin ya janye nasa da suke juyewa golden ʙwayar tsakkiya na zama siririya a wani irin salon yuuu ya ɗan lunshe su. Nima nawan na ɗauke da sauri ina haɗiyar wani yawu mai kauri dan gaba ɗaya jinai maʙogwarona ma ya bushe. Kofin ya ʙara miʙamin kansa a gefe, sai kuma ya miʙe.
         Haka kawai kallon nima yay matuʙar min tasiri a cikin jiki da ma jinina, dan haka na gagara sake kallon inda yake har ya buɗe ʙofar ya fita. Ajiyar zuciya mai nauyi na sauke tare da rumtse idanuna na cije lips da ʙarfi. Tea ɗin na cigaba da sha da ɗan zafi-zafi batare dana san abinda nake ba. A haka aka sake buɗe ʙofar, a zatona shine dan haka na gagara ɗaga ido na kalli wajen. Sai da mama Balki ta rangaɗa sallama sannan na ɗago da sauri fahimtar itace.
          Inda nake ta ʙaraso cike da tsokana take faɗin, ā€œA lallai ɗiyata ta fara samuwa. Yau kece da haɗa shayi da kanki batare dana sha fama ba kina bata fuska da korafin bakinki ba bu ɗanɗano. To UBANGIJI ya ʙara sauʙi.ā€
          A hankali nace Amin, dan a zatona bata haɗu da wannan pepper ɗin mutumin ba, sai naji hakan yamun daɗi. Sai dai me, bayan kamar mintuna biyar da zaman Mama Balki sai gashi ya sake dawowa tare da doctor. Miʙewa Mama Balki tayi fuskarta ɗauke da murmushi tana faɗin, ā€œHar an kammala Alhaji ʙarami?ā€.
          Cikin girmamawa, muryansa can ʙasa ya ce, ā€œEh mama sai ku shiryaā€. Jin abinda ya faɗa ɗin ya sani ɗagowa da sauri na kallesa. Sai muka haɗa ido. Da gudu na janye nawa na maida kan doctor dake min magana ɗan ji nake kamar ma kowa zai gane abinda ya faru tsakaninmu yanzu. Tambayoyi tamun tare da bani shawarwarin yanda zan kula da jikina yanda ya kamata har komai ya ʙarasa dai-daita. Duk bayan kwanaki biyu kuma zata zo har gida koni nazo asibitin za’a dinga sake dubani. Dan ba yau suka so sallamata ba. Sake ɗagowa nayi da mamaki sashen da yake. Yana tsayen dai har yanzu sai Mama Balki ce ke fita da kayayyakin mu tana dawowa alamar a iya ʙofa ake amsarsu. Yanda ya maida hankalinsa akan wayar hannunsa sai naji nutsuwa da alama baya jin duk abinda doctor ɗin ke faɗa. Taimaka min doctor tayi na sakko a saman gadon, hannunta riʙe da nawa ta ce, ā€œMuje ki ɗan tattaka ʙyaji daɗin ʙafafunki tunda kwana da kwanaki kina zaune waje ɗaya babu ko babban motsi. Kaina kawai na jinjina mata, ta ɗauki hijjab da Mama Balki ta ajiye sabo ta saka min da kanta. Har ʙasa hijjab ɗin ya kaimin kamar wanda nake amfani da su a gida. Sai naji daɗi sosai dan yaushe rabo. Ta gabansa mukazo muka gitta bai kallemu ba bai kuma motsa ba har sai da muka fice gaba sannan. Kusan Ę“ammatan Nurses ɗin nan da suka dinga kulawa dani dasu aka ɗunguma min rakkiya har gaban mota. Sosai motar tai min ʙyau, banyi tunanin yana bayanmu ba, sai da muka iso ina sallama da Nurses ɗin da doctor naga an buɗe masa ya shiga, ba’a rufe ʙofar ba alamar ni ake jira. Ji nai kamar na fasa kuka, dan hakan na nufin a kusa da shi zan zauna kenan. Babu yanda zanyi, dan doctor da kanta ta taimaka min na shiga. Sai da aka maida ʙofar aka rufe har Mama Balki itama ta shiga gaba an ma tada motar muna shirin barin asibitin sannan na lura da shegen karen nan nasa dake tacan jikin waccan ʙofar. Wani irin fasa ʙara nayi tare da daka tsalle na faɗa jikinsa a matuʙar firgice, bazaki gane yanda nake masifar tsoron kare ba wlhy Bilyā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’”š’Šš’™š’•š’†š’†š’

    ……Da uban sauri TJ ya taka birki dan shima firgita yayi, hakama Mama Balki, ya juyo zaiyi magana da sauri ya kauda kansa dan gaba ɗaya Samraah ta koma saman jikin ogan nasa ne. Mama Balki ma kallo ɗaya ta musu ta ɗauke kanta tana Murmushi. Shiko gogan tun faɗa masa jiki da tayi idanunsa kawai ya lumshe saboda ʙarar da tai har cikin tsakkiyar brain ɗinsa ya jita. Shi mutum ne da sam baya son hayaniya. Taɓasan da Laalah ya ɗan yi yana gurnani ya sa ya fahimci abinda take ma tsoro. Lumsassun idanunsa ya buɗe, ya ɗan kalli Laalah ɗin sai kuma ya kalleta. Tayi masifar cikuykuye sa daga ita har ʙatoton hujjab ɗinta. Shi sai abinma ya so bashi dariya. Amma sai ya danne baiyi ba.
            Cikin silent voice ɗin nan tasa yay kiran sunan TJ. Amsa masa yay da girmamawa, sai kuma ya buɗe motar ya fita. Kasancewar glass ɗin ta inda Laalah yake an saukesa ya sa ya ɗan duʙo ta wajen sai dai kansa a ʙasa ba kallonsu yake ba. Maimakon amsa masa sai ya ɗan shafa kan Laalah ɗin tare da furta, ā€œMaidashi wajen su Shu’aibuā€. Kaɗa bindi Laalah yay alamar dai yaji ubangidan nasa. Tj na buɗewa ya dira da kansa.
            Duk abinda suke ina jinsu. Ina jin ya fita na sauke ajiyar zuciya mai nauyi tare da zame jikina daga kan nasa. Ban yarda na kallesa ba na koma can jikin ʙofa na lafe. Ban kuma sake yarda na ɗago ba har muka iso gida. Sosai naji wani irin farin ciki da zaʙuwar ganin naje ga Ummie, dan bazan ɓoye miki ba har cikin tsakkiyar rai nake jin ʙaunar baiwar ALLAHr nan wlhy bily. ʘagara nayi motar ta tsaya, amma sai bata tsayan ba sai da akaje har ʙofar sashensa. Muna fitowa ina zumuɗin tafiya na koma waccan ʙofar Mama Balki ta dakatar da ni, magana na ɗago zanyi ta dakatar dani, tare da jan hannuna muka shige sashen nasa dan shi tuni yama shige abinsa. Mamaki ne ya kamani, yanzu kam kasa haʙuri nayi sai da nai magana kamar zanyi kuka.
             ā€œMama mi kuma zamuyi anan? Dan ALLAH mu tafi sashenmu ko wajen Ummieā€.
          Kanta tsaye ta ce, ā€œBanda ikon yanke wannan hukuncin Samraah. Sai dai mu jira daga bakin Alhaji ʙaramiā€.
        Sosai mamaki ya ʙara kamani, zan sake magana ta kama hannuna tai ciki dani. Zaune muka samesa a falo TJ na ajiye masa kofin coffee daketa tururi alamar yanzu nan ya haɗo masa shi. Tj ne ya amsa sallamar tamu, amma shi ko kallon ta inda muke ma baiyi ba. Wajen zama Mama Bilki ta nuna min, ban musa mata ba na zauna fuskata a kumbure. Kobi takaina batayi ba ta juya ta fita. A zatona wani abu zata ɗakko ta dawo, sai naji shiru har tsawon wasu mintuna. Ga TJ shima ya fice da ga ni sai shi. Karo na farko cike da ʙosawa na ɗaga kai na kallesa. Coffee ɗin sa yake sha hankali kwance tamkar ma bai san da zamana a wajen ba. Jinai raina ya sake ɓaci, amma sai na danne murya a sanyaye na ce, ā€œDan ALLAH zanje wajen Ummie na gantaā€.
           Kamar bai jini ba, sai da ya mula dan kansa sannan ya ɗan ɗago idanunsa ya kalla ta inda nake. Dai-dai na ɗan hararesa ni kuma batare da tunanin zai ɗago ɗin ba.
        ā€œOh hararata ma kike?ā€.
       Ya faɗa fuska a dake. Da sauri na marairaice fuskata kamar bani ba, cikin kalar tausayi na ce, ā€œNo ALLAH ba haka bane. Kawai an samu kuskure ne ni yazan hararekaā€. Na ʙare maganar a matuʙar karyar da kai. Ɗauke idanun nasa yay cike da basarwa ya cigaba da shan coffee ɗinsa. Naji tamkar na fasa ihu kona kamashi da duka. Amma duk babu dama. Sai kawai na dake tunda na fahimci Ę“an wulaʙancin ne a kansa….

            šŸŒœšŸ’®šŸŒ›

        Kamar kullum tsaff ta fito cikin gayunta. Arwa ce riʙe da handbag ɗinta tana mata shagwaɓar ta bata kuɗi. Itako sai faman latsa waya take tana tafiya kamar ma bata jin ɗiyar tata. Sai da suka gama sakkowa da ga upstairs ɗin sannan ta miʙa mata hannu alamar ta bata handbag ɗin. Sake marairaicewa Arwa tayi da maida hannunta baya ta ɓoye jakar. ā€œALLAH Ummy ni bazan baki ba, just 200k fa nake so bawani kuɗi masu yawa ba. Gift da zan sayama Lubnah yau birthday ɗinta. Kuma motana fa nace miki duk friend ɗina sun sanni da shi, dan ALLAH ki bani baʙin naki, ALLAH bazanyi tuʙin banza ba i promise ā€.
           ā€œRiʙe promise ɗinki. Dan bazan baki motana ba. Ga dai 100k nan na saka miki je kiyi manage da shi banda kuɗi yau. Give me my bag jare. Kuma ki tabbatar kin dawo gidan nan kafin ten na dare. Dan karna shigo ban sameki ba. Zan ɓata miki raiā€.
        Baki cike da iska Arwa ta miʙa mata handbag ɗin, babu ko godiya ta juya fuuuu ta koma sama. Kai kawai Hajiya ʙarama ta girgiza ta juya tai tafiyarta. Babu kowa a falon sai su A’i dake gyarawa. Gaisheta sukeyi cike da girmamawa. Itako tana amsa musu a nutsen nan nata babu alamar hayaniya a tattare da ita. Daka ganta kaga mace mai haʙuri da iya zama da mutane. Compaund ta fita, kai tsaye tai wajen motarta dan ita sam bata da driver. Bata yarda da kowa ba ita ke tuʙa kanta, tana ʙoʙarin ajiye handbag ɗinta a side ɗin mai zaman banza dai-dai nan Hajiya Mammah ke fitowa itama cikin wani shegen shiga na manyan mata dake ji da kansu. Kallon juna sukai, amma sai Hajiya Mammah ta watsar da Hajiya ʙaramar tamkar bata ganta ba ma. Lips Hajiya ʙarama ta cije tare da faɗin, (zanyi maganinki ne) a zuciyarta. A zahiri kam sai ta saki murmushi tare da nufar Hajiya Mammah ɗin cikin girmamawa ta gaisheta. A ɗage Hajiya Mammah ta amsa tana ʙoʙarin shigewa motar da drivern ta ya buɗe mata. Itama sai Hajiya ʙaramar tai murmushi ta juya ga tata motar ta shiga. Kusan a tare suka fice a gidan. Sai dai suna fitowa babban titi kowa yay hanyarsa. Ita Hajiya Mammah gidan Baba prof ta nufa, itako Hajiya ʙarama asibiti ta nufa…

              ⭐⭐⭐

          Gidane babba mai ʙyau kuma sosai. Ga masu aiki tako ina nakai kawo maza kai kace akwai wasu mutane da yawa a ciki. Guri drivern Hajiya Mammah ya samu yayi parking, sannan ya fito cikin rawar jiki ya buɗe mata, sai faman cika take da batsewa wa ma’aikatan dake ta faman gaisheta da girmamawa. Ko sau ɗaya bata amsa musu ba, sai ma tana fitowar tuni wani yazo ya amshi handbag ɗin hannunta dan sun san halinta sarai. A yatsine take bin jibga-jibgan motoci ukun dake fake a compaund ɗin wanda bata san da su ba a gidan da kallo. Cike da isa ta dubi wanda ya amsa mata bag ɗin ta ce, ā€œWaɗan nan motocin fa?ā€.
             Muryarsa har rawa take wajen bata amsa da, ā€œNa baʙine da Alhaji yayi ranki ya daɗeā€.
         ā€œBaʙi?ā€.
      Ta maimaita da sigar tambaya, sai dai kuma kafin ya bata amsa tayi gaba bakinta a taɓe. Bayanta yabi da sauri. Kanta tsaye ta shiga ta main perlor ɗin gidan ta shiga ainahin falonsu. Babu kowa a ciki, sai ʙamshin air fresheners dake tashi da kuma ɗan sanyin ac kamar ba safiya ba. Baba kam akwai son tsafta. Duk da rayuwarsa yake shi kaɗai a gidan babu mace zaka samu komai tsaf-tsaf. Dan tunda mahaifiyarsu ta rasu bai sake aure ba. Suma kuma ko yace zai yi ɗin bazasu bariba wlhy. Dan yanda ba’ama uwarsu kishiya tana raye ba bayan ta mutu ma baza’ai mata ba. Zaune takai saman luntsuma-luntsuman kujerun falon. Tuni ta wani lume a ciki dan sunada bala’in taushi. Baban nasu ɗan gata ne, dan duk shekara sai Awwab ya canja komai na gidan an sake masa sabon fenti. Kukun gidan daya fito ne yana gaidata ya katse mata tunani, a ɗage shima ta amsa masa fuska a yamutse. Har zai juya ta dakatar da shi, umarnin haɗa mata breakfast ta bayar. Cike da girmamawa ya amsa mata yana komawa ciki. Babu jimawa kuwa ya kammala komai ya kawo ya ajiye gabanta. Zama ta gyara da ʙyau ta fara kwasar girki tana chart da Rubayya dake ʙara tsara mata yanda zata tunkari Baban. A haka Baba prof ya shigo falon ya sameta. Kanta dake duʙe ta ɗago ta kallesa, yana sanye cikin farar jallabiya tas data ʙara fiddo tsufarsa. Dan bashi da wani jikin kirki, gashi dogo masha ALLAH kamar dai su Paah dan duk shi suka biyo har su Maash duk tsahonsa ne. Kanta ta ɗan rissinar tare da faɗin, ā€œBarka da fitowa Babaā€.
           ā€œYauwa Nafisatu kece a gidan?ā€.
        Ya faɗa yana kaiwa zaune. Murmushi tayi, tare da sake rissinawa ta shiga gaishesa. Da kulawa ya amsa mata yana tambayarta mutanen gidan da jikin Ummie. Cikin ɗan ɗage kafaɗa ta ce, ā€œDa sauʙi to Baba. But ba shiga nake ba dan tun dai randa ta faɗin nan gaskiyaā€.
        Fuskarsa a ɗan ɗaure yace, ā€œBan gane ba?ā€.
          Fahimtar katoɓarar da tayi yasa ta ɗan ʙaryar da kai gefe. ā€œBaba ba wani abu nake nufi ba fa. Wlhy ina jin tsoro ne shiyyasa. Kasan idan Ummu-Hidaya na’a wannan yanayin akwai haɗari shiga inda takene. Amma nasan da sauʙi gaskiya, tunda kaga ba’ai kiranka baā€.
            Kansa ya jinjina cikin nuna gamsuwa. Ita kuma ta sauke numfashi. Sai kuma tayi murmushi da sake ɗan dubansa. ā€œBaba wai motocin suwaye na gani haka a gidan nan?ā€.
         Hannunsa ya ɗan yarfar da taɓe baki, sai kuma ya ɗauka black tea ɗin da kuku ya kawo masa ya fara kurɓa, sai da yay kusan sau uku kafin ya kalleta. ā€œShugaban jam’iyyar ACC ne na ʙasa da wasu ministoci guda biyu. Suna damuna a kwanakin nan akan son na shiga siyasa. Ni kuma abinda bai taɓa birgeniba kenan Nafisatu. Yanzu ma shugaban ʙasa ne da kansa ya turosu. Ni dai na faɗa musu gaskiya ina akan bakana. Amma sun dage matuʙa. Shine nace suje zanyi shawaraā€.
           Cike da zumuɗi da zamala Hajiya Mammah ta gyara zamanta. Gaba ɗaya 32teeth ɗinta washe suke. ā€œAmma Baba mizai hana ka amshi tayinsu. Ni banga wani aibu ba a siyasa ai. Sannan kowane irin sharuɗɗa ka cikasu da ko ɗar bazakaji na shiga ba. Tayinfa kujera suke maka mai matsayin farko a jihar nan. Zamu kasance cikin matuʙar farin ciki a kiramu first family na wannan state mai girma irin Lagos. Baba dan ALLAH ka amsaā€. Ta ʙare faɗa cikin shagwaɓa. Ajiyar numfashi ya sauke tare da gyara zamansaā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’”š’†š’—š’†š’š’•š’†š’†š’


    …….Tsahon lokaci muna zaune shiru batare da ya sake magana ba. Coffee ɗinsa kawai yake sha a hankali yana kuma daʙilar tab da ke a saman ʙafarsa da yay crossing.
              ā€œWane hukunci kika yanke?ā€.
         Tambayarsa ta iso cikin kunnena a bazata. Ɗan ɗagowa nayi na kalla inda yake, dan da farko ma banyi zaton shine yay maganar ba. Yanzu ɗin ma daʙilar tab ɗin kawai yake, dan haka na ce, ā€œWai kaine kayi tambaya?ā€.
       Ɗago manyan idanunsa yayi a hankali ya kalleni. Sai kuma ya sake maidasu kan abinda yake yi. A taʙaice ya ce, ā€œUhmmā€.
        Ajiyar zuciya na sauke da faɗin, ā€œOkay. Amma ban gane tambayar ba. Akan mi kake nufi?ā€.
          ā€œKomai!ā€.
       Ya faɗa can ʙashan maʙoshi. Jimmm kawai nayi ina tunani bayan na sake maimaita komai ɗin a zuciyata. Kai gaskiya ban gane ba, dan duk da ina zargin ahalinsa ai nake ga bai dace na fito fili na nuna ba, tunda ba sanin nasan tarihin gidansu yay ba. Gara idan shine ya sanar min wani abu ai. Fuska na marairaice a sanyaye na ce, ā€œALLAH kuwa Ya Awwab ban gane baā€.
         Komai baice min ba. Yanzu ma ko ɗagowa ya kalleni ɗin baiyi ba. Kusan mintuna biyu ya ajiye kofin coffee ɗin da yake sha sai kuma ya gyara zamansa. Da hannu yay min alamar nazo. Idanu na waro masa alamar mamaki, amma sai ya ɗauke kansa cike da basarwa yana sake tsuke fuska. Banda zaɓin daya wuce bin umarninsa. Dan sam bazan iya musa masa ba. Ina jinsa da wani irin girma da kima fiye da ko yaushe a yanzu. Sannan wani irin shakkarsa nake ji, kwarjinin sa gaba ɗaya ya cika falon har ina jin yama mana kaɗan. A hankali na miʙe kamar wadda tai laifi take tsoron duka. Dan da sanɗa na isa gabansa. ʘoʙarin kaiwa ʙasan carpet nake ya min nuni da saman cinyarsa. Kaina na maʙe masa alamar a’a, sai ya ɗan taɓe baki ya nuna gefensa batare da yayi magana ba. Dole na canja na koma kan kujerar gefensa dai na zauna. Sai kuma na ɗan saci kallonsa ta gefen ido. Da sauri na maida kaina ʙasa dan dai-dai shima yana ɗagowa ne. Wani irin ratsawa muryarsa ta sake min har cikin kaina, duk da kuwa yayi maganar ne ba cikin tsawa ko hayaniya ba, dan ko a falon kake ba lallai ka jisa ba dan nima na kasance gab da shine. Amma ban sani ba, kodan sai da ya kamo yatsun hannuna cikin nashi tattausan hannun ne sannan yay magana oho. Sake matsa yatsun nawa yay a hankali ina kuma jin kaifin idanunsa har cikin jijiyoyin da jinina ke yawo.
          ā€œIdan nace komai ina nufin ina nufin komai da komai. Nasan zuwa yanzu kin san wanene Awwab a zahirance da baɗinance. Dan kinji komai a wajen Mama, kin kuma san komai a makwancinsaā€.
          Da sauri na ɗago ina ware idanuna duk da zancensa na ʙarshe ya bani kunya. Cikin ɗan rawar lips da nuna mamaki na ʙarara akan fuska na ce, ā€œYa akai ka sani mama ta faɗa min?ā€.
        Wani ɗan makirin murmushi ya sakar min da lumshe idanunsa sai kuma ya buɗesu luuuu ya zuba su a cikin nawa. ʘyaʙyʙyafta idanu na fara da ʙoʙarin janye yatsuna dake a cikin nasa har yanzu. Amma sai ya hana hakan ta hanyar sake riʙesu da ʙyau yana girgiza min kansa. Sai kuma ya janye idanun kamar a kasalance ya ɗaura yatsarsa manuniya mai ɗauke da dogon farce fari tass har wani ʙyalli yake tsabar yanda yake fes, akan zobena ya saka yatsan yana wani zagayawa. Zoben na kalla da sauri nima dan sam ban gane inda ya dosa ba. Sai da ya gama zagayesa sannan ya zaresa a hankali daga cikin yatsata. Ɗan jujjuya min shi yay akan fuska, sai kuma ya runtsesa a cikin hannunsa yana kallona gira ɗaya a ɗage.
          ā€œKe yarinya ne Samrh, tsiwanne kawai yayi miki yawa da shegen kauɗi. Shin bakiyi tunanin taya akai kika zo gidan nan ba haka kai tsaye bayan kin gudu min? Nasan hakan zai iya faruwa, amma dai abune da zai zama mai wahalar gaske musamman idan mukai duba da hannun da kika faɗa….ā€
        Kasa haʙuri nayi, cikin tare numfashinsa na furta, ā€œDama da saninka nazo nan gidan ke nan?ā€.
               Idanu ya ɗan lumshe ya sake buɗewa a kaina. A bazata naji saukar hannunsa kan hancina. Ya ɗan jashi kaɗan da faɗin, ā€œYanda kike stubborn ɗin nan ai sai da kula. In ba hakaba zaki ɓaro min aiki ne Ę“ar jaridaā€.
         Duk da naji kunya sai da na ɗan tura masa baki. A shagwaɓe na ce, ā€œAi ALLAH kaine stubborn a gidan nan. Ni dama nata wasi-wasi, duk da nasan kaɗan daga ikon UBANGIJI hakan ta kasance. Amma dan ALLAH Ya Awwab ya akayi nazo?ā€.
          Shiru yayi kamar bazai tanka min ba. Sai da na marairaice masa kamar zanyi kuka sannan. Yana a kwancensa jikin kujera idanunsa a lumshe yanzu. Hakan ya bani damar zuba masa idanuna ina kallon yanda yake motsa lips kamar abin dole. ā€œTun a guduwan farko nasan zaki iya maimaitawa. Shiyyasa na samar da zoben nan exactly irin naki ta yanda zan san duk wani motsinki. Kina asibiti a Abuja na sa miki, bayan dinga nuna kin inda kike har magana idan akayi ko kikayi zan iya jinkiā€. Ya ʙare maganar yana nuna min abinda ke a kunnensa kamar bluetooth sai dai shi ʙarami ne bai kai bluetooth girma ba
            Cikin ɗan yarfar da hannu da mamaki na ce, ā€œBala’i, dama kaje asibiti ka duba ni ne? Wlhy naci kai. Taya ban taɓa ma lura da zoben nan ba nawa bane?ā€.
         Idanu ya ɗan buɗe yana kallona. Kamar bazai ce dani komai ba sai kuma ya motsa small pinkish lips ɗinsa a hankali. ā€œSaboda ke yarinya ceā€.
       Jinai kamar na harararesa amma bazan iya ba. Sai wani cemin yarinya yake. Amma duk da haka sai da na ɓata fuska. Hannu na miʙa masa na ce, ā€œBani zoben na gani dan ALLAHā€.
          Idanunsa ya maida ya lumshe. A taʙaice ya furta, ā€œYa gama aikinsa. Ina jinki mi kika yanke dan bani da lokaci zanyi baʙiā€.
            ā€œNi ban yanke komai ba, akan samun lafiyar Ummie kawai nake da plansā€.
       Idanu ya buɗe sosai yana kallona. Sai na ɗauke nawa daga kallonsa dan bazan iya jurewa ba. A hankali kamar mai jin tsoro na furta, ā€œYa kamata Fahad ya dawo gida kamar yanda kowa yake gidaā€.
           ā€œNooo!!ā€.
       Ya faɗa a tsawace yana ʙoʙarin miʙewa. Duk da yanda ʙirjina ya buga da rawar da jikina yake yi sai da nai saurin kamo hannunsa. Muryata a karye kamar zanyi kuka na ce, ā€œDan ALLAH kayi haʙuri ka zauna. Bafa kaji ʙarshen maganata ba Pleaseā€.
         ʘin zaman yay har tsawon lokaci. Sai faman huci ma yake yi abin mamaki da tsoro. Hatta da gashin jikinsa duk sun mimmiʙe. Muryata na rawa cike da magiya na sake faɗin, ā€œDan ALLAH dan ALLAH. Burinka fa shine samun lafiyar Ummie, kuma wannan hanyar da zan faɗa maka in sha ALLAHU ina fatan zata taimaka mana. Kayi haʙuri ka danne duk abinda kake ji game da ɗan uwanka. Dan wlhy komai bazai yiyu ba sai mun haɗa ʙarfi da ʙarfe. Ni, kai, shi, Hayatu, Mama, Baba, da duk wanda ka aminta da shi a cikin yaranka. Idan har wanda baka haɗa komai da su a duniya ba zasu ci arziʙinka yanda suke so har su bama Ę“an uwansu kai mi kake jira akan naka gudan jinin ɗaya tilo. Kana ganin idan lafiyar Ummie ʙalau zata barku a cikin wannan halin? Ko a yanzu da take a cikin halin jarabawa wlhy maybe tana jin zafi da kewar rashin ganin ɗan uwanka dan bata san taya zata furta bane kawai. Karfa ka manta shima nan gidansu ne Ya Awwab. Yanda kake da iko da komai na cikinsa shima haka yake da iko da shi dan ko’a addinance matsayin magada masu kaso kai ɗaya kuke amsawa. Duk duniya fa baka da kamarsa, kamar yanda shima baida kamar ka. Duk mu ɗin nan da muke zagaye da kai son zuciya ko wani dalili zai iya sakawa mu gujeka, amma shi komi ka zama bazai daina jin ʙaunarka a zuciyarsa kamar yanda kaima nasan kana ʙaunarsa. Wannan ʙiyayyar dake tsakaninku ʙirʙirarriyar ʙiyayya ce, kune kuma ya kamata kuyi yaʙi da zukatanku wajen ganin kun canjama abokan gaba nasararsu. Kaifa ka tunatar dani ba’aima maʙiyi gaggawa, idan ba haka ba zai rigaka kai inda kake hari harma ya juyo kai baka kai ba. To kenan in har zaka tafin sai ka kasance mai kula gudun kar ya saka maka tarkon da zai riʙeka ya hanaka isar kafin shi ɗin ya iskoka kuma. Dawowar Fahad gidan nan shine first target ɗin mu akan kowa da komai wlhy. Amma na baka dama kaje kayi tunani ka gani, sannan ka nema zaɓin ALLAH. Ni kuma na maka alʙawarin duk abinda ka yanke zanyi biyayya a kansa sai muje plan na gaba, ni dai fatana kawai Ummie ta samu lafiya neā€. Daga haka na saki masa hannu a hankali. Kaina na duʙar na saki kuka. Dan harga ALLAH yanzu wani masifar tausayi yake bani. Bawan ALLAHn nan yana cikin wani irin bahagon ʙulli ne mai tsaurin gaske. Shiyyasa aketa amfani da shi ana azabtar da mahaifiyarsa da ɗan uwansa. Nayi zaton tafiyar tasa zaiyi, sai naga a hankali ya koma ya zauna cikin kujerar tare da dafe kansa da duka hannayensa yay masifar cije ɗan ʙaramin lips ɗinsa kamar zai hudashi da haʙori. Ha jima a haka kafin ya ringa sauke wasu irin zafafan huci da naji ʙarin tsoronsa a raina. Dan tuni na maʙure a cikin kujera kamar mage taga ʙare a lungun mai hanya ɗaya talā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’†š’Šš’ˆš’‰š’•š’†š’†š’

    …….Mun jima zaune a hakan kafin ya mike a fusace. Taku ɗaya biyu ya tsaya cak, batare da ya juyoba cikin kaushin murya ya furta, ā€œDaga yau zaki cigaba da zama ananā€.
             Wani irin zabura nayi yan hanjin cikina na wantsalawa tare da bugun zuciyata. Bamma san sanda na furta, ā€œAnan kuma?ā€. Ko kallon inda nake baiyi ba yayi wucewarsa hanyar bedroom ɗinsa. Wani irin bugawa zuciyata keyi diff-difff!! Dan har ga ALLAH maganar tashi tayi masifar ratsa min ʙashi da bargo. Wane irin neman bala’ine haka dan ALLAH. Taya zan cigaba da zama a side ɗinsa bayan Mama Balki ta sanar min babu wanda yasan akwai aure tsakanina da shi. Sannan yan uwansa ma abinda ya faru kallonsa suke ama tsayin fyaɗe. ā€œNa shiga uku ni Samraah mutumin nan zai kasheni. Ni wlhy koma ba duk wancan ba bazan iya zaman anan da shi mu biyu kacal ba. Mutumin daya nema kusan kasheni ina gaskiya bashi yiwuwa. Gara ma tun kan wankin hula ya kaini dare na kama gabana. Inama laifin yace na koma sashen Ummie dan ALLAH. Zaram na miʙe, har haɗawa nake da sassarfa na nufi ʙofar fita. Sai dai kuma gam take alamar an kulle. Idanuna ne suka cika da ʙwalla. Ji nake kamar na saki ihu. Na jima a wajen kafin na yanke shawarar zuwa na bashi haʙuri tare da fahimtar da shi illar wannan hukuncin nasa dan bazai haifar mana da ɗa mai ido ba daga ni har shi ɗin….
                
    šŸŒœšŸŒœšŸ’®šŸŒ›šŸŒ›
        

      ā€œNafisatu ai ba amsar bane matsalar. Maganar kuma zamowarmu kuma family na farko a jihar nan a tunanina tuni muna ɗaya daga cikin masu wannan matsayin ama Nigeria ba jihar Lagos ba. Ɗanki ya jima da samo mana wannan sunan ama duniya ba'a ʙasar haihuwarmu kawai ba. Siyasa ta wuce duk yanda kike tunani, cike take da rikice-rikice da matsaloli iri-iri. Bazaki gane hakan ba sai mun farata. Amma dai ki bari zan tattauna da Awwab. Kin sanshi yanada experience akan irin waɗan nan abubuwanā€.

           ā€œBaba yanzu nan duk mu yawan yaranka har mu huɗu cif babu wanda zaka iya shawara da shi a shekarunmu sai jika. Awwab har wani hankaline da shi wanda ko aure baiyi ba.ā€
        ā€œHumm Nafisatu, aure ai lokacine da shi ko?ā€.
              ā€œBaba yana da lokaci, amma kuma kaima ya kamata ka motsashi, yanzu irin wannan abun daya faru idan da maganar nan ta fita mi muke tunani? Ni yanzu ma tsorona ALLAH tsorona yaji daɗi ya cigaba da aikatawa tunda ba kunya garesa ba. Ballema yaga ba’a ɗauki wani mataki ba akai ai kaga abun bamusan kuma ina zai tsaya ba. Tun fa yana taɓa Ę“an aiki wlhy wataran kan ʙannensa zai dawo. Dan Awwab yariga yayi gaurin da macen kawai yake buʙata fa. Ya kamata a duba wannan zancen Baba. Idan yana akan bakansa shi baiga wadda yake so ba ai ga Ę“ar uwarsa nan Azizat. A haɗasu mana kawai tunda Ita dai bazataʙi bin umarninmu ba. Shima kuma idan yaga kowa yaʙi saurarensa ai dole ya amince a wannan karon tunda koba komai yana son asirinsa ya rufu kar duniya ta saniā€.
            Jinjina kai kawai Baba yake. Sai da takai har ʙarshe sannan ya nisa. ā€œShawararki abar dubawace Nafisatu, kuma zan duba. Awwab ɗinne sai a hankali, yaro ne mai shegen taurin kan tsiya. Yanzu fa ki duba ki gani saboda yasan abinda yay ba dai-dai bane sam yaʙi zuwa gidan nan. Idan naje can duk yanda zai zame ya gudumin ya sani. Amma barshi nasan mi zanyi. Zanzo yau da dare na ritsashi in sha ALLAHU. Da zarar ya shigo gida ki kirani kawaiā€.
         Cike da farin ciki Hajiya Mammah ta amsa da, ā€œTo in sha ALLAHU kuwa Baba. Amma maganar siyasar nan itama dai dan ALLAH a duba mana. Yaya kaga Nafisatu Adams K/Mashi ɗiyar gwamnan jihar Lagosā€.
        Yanda tai maganar tasa baba ʙyalʙyalewa da dariya. Itama dariyar takeyi….

            ā¤ļøā¤ļøā¤ļøā¤ļø

          Kamar mai tsoron a jita a hankali nai knocking ʙofar, shiru babu motsin komai. Sake yi nayi har fin sau uku. Ganin dai bazai kulani ba na yanke shawarar buɗewa kawai ma shiga. A hankali na murɗa handle ɗin kuwa. Sai ko gashi ya buɗe. Sai da na sauke ajiyar zuciya tare da tsayawa na daidaita kaina sosai sannan na tura na shiga da sallama. Turus na tsaya ina kallonsa dan zaune yake akan sofa daga shi sai towel da waya a hannunsa yana magana cikin yanayin nan nasa a daʙile kamar wanda akama dole. A hankali na maida ʙofar na rufe ina mai duʙar da kaina dan bazan iya jurar kallonsa a yanda yake ba. Nafi minti biyu a wajen ina sauraren wayar tasa dana fahimci da Hayatu yake yinta. Sai dai abinda ya ɗan ja hankalina jin yana faɗin idan sun huta Hayatun ya kawosu nan gida. To ko su waye keda irin wannan matsayin haka. Dan na fahimci tunda nazo gidan nan ban taɓa ganin wani baʙo daya shafesa ba yazo. In banda ranar birthday ɗin nan da Bahijja tace min wanda suke zaune a waje ɗaya abokansa ne, kuma duk ba’a ʙasar suke ba idan ka cire ɗan sarkin Lagos ɗin. Ganin har ya kammala ya miʙe yana ʙoʙarin nufar mirror ya sani gyara tsaiwata. Dan ya wani basar tamkar baima ganni ba. Kuma na san yasan na shigo ɗin rainin hankalinsa ne kawai. Kaina a ʙasa daga ʙofar ɗakin na furta, ā€œDan ALLAH ina son muyi maganaā€.
        Bai tanka min ba, bai kuma fasa abinda yake ba. Sai da ya mula dan kansa kusan minti biyu sannan ya magantu. Cikin silent voice ɗin nan tasa a daʙile ya furta, ā€œKi wuce wanka baʙi zasu shigoā€.
            Ji rainin hankali, ina masa wata maganar yana min wata. To ina ruwana da wasu baʙinsa. A zahiri kam sai na ʙara sauke murya har lokacin kan nawa a ʙasa. ā€œDan ALLAH kayi haʙuri ka barni naje can inda na saba. Ko kuma na koma sashen Ummie tunda dama a yanzu kusan acan ɗin nake. Ya Awwab taya zan dawo nan bayan kasan akwai matsala. Babu fa wanda yasan akwai wani maganar aure a tsakaninmu a gidan nan. Mi kake tunani zasu fassara zaman nawa?ā€.
           ā€œSu fassara duk yanda yay musu! Idan kuma kina buʙatar su sanin ne, yanzun nan sai na tarosu su saniā€.
        Da sauri na ɗago ina kallonsa. Yanda yay maganar kansa tsaye babu wani alamun ya ɗauki zancena da muhimmanci. Kai wlhy stubborn mutumin nan ya fara isata. Da ʙyar na iya dannewa muryata na ɗan rawa na ce, ā€œIdan kai zaka iya fuskantar su ka kuma ɗauka komai wlhy ni bazan iya ba. Sannan ba wannan rigimar nake so ba yanzu lafiyar Ummie ce damuwata. Dan ALLAH ka duba zance na yana da muhimmanciā€¦ā€
            ā€œKin dameni Madam wuce wanka kafin nazo kankiā€.
        Ya faɗa da ɗan kaushin harshe yana ajiye cumb ɗin hannunsa yana barin wajen. Karan farko naji hawaye sun gangaro min.
          ā€œKarna fito na sameki a wajenā€.
      Ya sake faɗa dai-dai yana shigewa cikin cikin closet ɗinsa. Hannuna na dunʙule kamar zan kaima bango naushi sai kuma na tausayama kaina dai. Dan nasan nice zan sha wahalar a ʙarshe hannunna ya rugurguje a banza. Hararar inda ya shige ɗin nayi ina cizar lips ɗina da ʙarfi, ga hawaye share-share a fuskata. Jin motsin kamar zai fito ya sani zabura na nufi bathroom ɗin. Dole ina ji ina gani na haɗa ruwan wankan nai ʙoʙarin fara yi. Wankan nake ina hawaye da hango irin bala’in da zai iya biyo baya. Dan wlhy abin bazai zama mai sauʙin ba a gareni. Gara sashen Ummie da nake zama shi wannan suna ganin ai kamar ina cutuwane shiyyasa aka ɗagamin ʙafa. Amma nan fa? Ni kaina idan an titsiyeni ban san mizan ce ba. Dan nayi alʙawarin in har bada kansa ya fito ya bayyana musu wacece ni ba wlhy ko za’a kasheni bazan faɗa ba. Sai da na kammala wankan sannan hankalina ya tashi, dan ban san yaya zanyi da kayan sakawa ba kuma. Bathrobe ɗin sa na ɗauka na saka. Sallar walha da nake son zuwa nayi dan lokacinta yayi ya sani haʙura na fito, amma sai da na leʙa cikin ɗakin sannan. Shiru babu motsin komai, sannan a iya hangena ban hango alamar akwai mutun ba. Ɗan ajiyar zuciya na sauke na fito a ɗan ɗarare. Nannauyar ajiyar zuciya na sauke ganin tabbacin baya ɗakin, tunanin sauri na shafa mai yazo min, dan haka na nufi gaban mirror ɗin nashi. Zama nayi tare da bin kayan dake akai da kallo, cikin ɗan taɓe baki na furta, ā€œSai kace maceā€. Da ʙyar na iya gane man shafawa, ina son na fara dubashi ina tsoron yin jinkirin da har zai dawo ya saman a wajen. Da sauri-sauri na shafa man da duk abinda zan iya amfani da shi a wajen. Na miʙe raina fal tashin hankalin kayan daya kamata ace na saka ya shigo. Daburcewa nayi dan abin yazo min a bazata. Rasa makamar riʙewa ta sani komawa kan stool ɗin kujerar na zauna tare da duʙar da kaina. Baiyi magana ba, sai madaidaicin akwati da yazo ya ajiye gab dani. Juyawa yay yayi ficewarsa yana faɗin, ā€œZanje wajensu, da munyi salla zasu shigo. Zaki iya zuwa duba Ummien kafinā€. Daga haka yay ficewarsa. Da kallo na bisa duk kaina duk a ɗaure. Sai dai furta zan iya zuwa duba Ummie ne yay matuʙar wanke min zuciya. Mikewa nai cike da zumuɗi harda daka tsalle dan farin ciki, tuni na nema damuwata da tunanin wasu baʙi da ya ishi mutane da zancensu na ɗauki akwatin daya ajiye ɗin. Saman gado na kaisa na buɗeā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’†š’Šš’ˆš’‰š’•š’†š’†š’

    …….Mun jima zaune a hakan kafin ya mike a fusace. Taku ɗaya biyu ya tsaya cak, batare da ya juyoba cikin kaushin murya ya furta, ā€œDaga yau zaki cigaba da zama ananā€.
             Wani irin zabura nayi yan hanjin cikina na wantsalawa tare da bugun zuciyata. Bamma san sanda na furta, ā€œAnan kuma?ā€. Ko kallon inda nake baiyi ba yayi wucewarsa hanyar bedroom ɗinsa. Wani irin bugawa zuciyata keyi diff-difff!! Dan har ga ALLAH maganar tashi tayi masifar ratsa min ʙashi da bargo. Wane irin neman bala’ine haka dan ALLAH. Taya zan cigaba da zama a side ɗinsa bayan Mama Balki ta sanar min babu wanda yasan akwai aure tsakanina da shi. Sannan yan uwansa ma abinda ya faru kallonsa suke ama tsayin fyaɗe. ā€œNa shiga uku ni Samraah mutumin nan zai kasheni. Ni wlhy koma ba duk wancan ba bazan iya zaman anan da shi mu biyu kacal ba. Mutumin daya nema kusan kasheni ina gaskiya bashi yiwuwa. Gara ma tun kan wankin hula ya kaini dare na kama gabana. Inama laifin yace na koma sashen Ummie dan ALLAH. Zaram na miʙe, har haɗawa nake da sassarfa na nufi ʙofar fita. Sai dai kuma gam take alamar an kulle. Idanuna ne suka cika da ʙwalla. Ji nake kamar na saki ihu. Na jima a wajen kafin na yanke shawarar zuwa na bashi haʙuri tare da fahimtar da shi illar wannan hukuncin nasa dan bazai haifar mana da ɗa mai ido ba daga ni har shi ɗin….
                
    šŸŒœšŸŒœšŸ’®šŸŒ›šŸŒ›
        

      ā€œNafisatu ai ba amsar bane matsalar. Maganar kuma zamowarmu kuma family na farko a jihar nan a tunanina tuni muna ɗaya daga cikin masu wannan matsayin ama Nigeria ba jihar Lagos ba. Ɗanki ya jima da samo mana wannan sunan ama duniya ba'a ʙasar haihuwarmu kawai ba. Siyasa ta wuce duk yanda kike tunani, cike take da rikice-rikice da matsaloli iri-iri. Bazaki gane hakan ba sai mun farata. Amma dai ki bari zan tattauna da Awwab. Kin sanshi yanada experience akan irin waɗan nan abubuwanā€.

           ā€œBaba yanzu nan duk mu yawan yaranka har mu huɗu cif babu wanda zaka iya shawara da shi a shekarunmu sai jika. Awwab har wani hankaline da shi wanda ko aure baiyi ba.ā€
        ā€œHumm Nafisatu, aure ai lokacine da shi ko?ā€.
              ā€œBaba yana da lokaci, amma kuma kaima ya kamata ka motsashi, yanzu irin wannan abun daya faru idan da maganar nan ta fita mi muke tunani? Ni yanzu ma tsorona ALLAH tsorona yaji daɗi ya cigaba da aikatawa tunda ba kunya garesa ba. Ballema yaga ba’a ɗauki wani mataki ba akai ai kaga abun bamusan kuma ina zai tsaya ba. Tun fa yana taɓa Ę“an aiki wlhy wataran kan ʙannensa zai dawo. Dan Awwab yariga yayi gaurin da macen kawai yake buʙata fa. Ya kamata a duba wannan zancen Baba. Idan yana akan bakansa shi baiga wadda yake so ba ai ga Ę“ar uwarsa nan Azizat. A haɗasu mana kawai tunda Ita dai bazataʙi bin umarninmu ba. Shima kuma idan yaga kowa yaʙi saurarensa ai dole ya amince a wannan karon tunda koba komai yana son asirinsa ya rufu kar duniya ta saniā€.
            Jinjina kai kawai Baba yake. Sai da takai har ʙarshe sannan ya nisa. ā€œShawararki abar dubawace Nafisatu, kuma zan duba. Awwab ɗinne sai a hankali, yaro ne mai shegen taurin kan tsiya. Yanzu fa ki duba ki gani saboda yasan abinda yay ba dai-dai bane sam yaʙi zuwa gidan nan. Idan naje can duk yanda zai zame ya gudumin ya sani. Amma barshi nasan mi zanyi. Zanzo yau da dare na ritsashi in sha ALLAHU. Da zarar ya shigo gida ki kirani kawaiā€.
         Cike da farin ciki Hajiya Mammah ta amsa da, ā€œTo in sha ALLAHU kuwa Baba. Amma maganar siyasar nan itama dai dan ALLAH a duba mana. Yaya kaga Nafisatu Adams K/Mashi ɗiyar gwamnan jihar Lagosā€.
        Yanda tai maganar tasa baba ʙyalʙyalewa da dariya. Itama dariyar takeyi….

            ā¤ļøā¤ļøā¤ļøā¤ļø

          Kamar mai tsoron a jita a hankali nai knocking ʙofar, shiru babu motsin komai. Sake yi nayi har fin sau uku. Ganin dai bazai kulani ba na yanke shawarar buɗewa kawai ma shiga. A hankali na murɗa handle ɗin kuwa. Sai ko gashi ya buɗe. Sai da na sauke ajiyar zuciya tare da tsayawa na daidaita kaina sosai sannan na tura na shiga da sallama. Turus na tsaya ina kallonsa dan zaune yake akan sofa daga shi sai towel da waya a hannunsa yana magana cikin yanayin nan nasa a daʙile kamar wanda akama dole. A hankali na maida ʙofar na rufe ina mai duʙar da kaina dan bazan iya jurar kallonsa a yanda yake ba. Nafi minti biyu a wajen ina sauraren wayar tasa dana fahimci da Hayatu yake yinta. Sai dai abinda ya ɗan ja hankalina jin yana faɗin idan sun huta Hayatun ya kawosu nan gida. To ko su waye keda irin wannan matsayin haka. Dan na fahimci tunda nazo gidan nan ban taɓa ganin wani baʙo daya shafesa ba yazo. In banda ranar birthday ɗin nan da Bahijja tace min wanda suke zaune a waje ɗaya abokansa ne, kuma duk ba’a ʙasar suke ba idan ka cire ɗan sarkin Lagos ɗin. Ganin har ya kammala ya miʙe yana ʙoʙarin nufar mirror ya sani gyara tsaiwata. Dan ya wani basar tamkar baima ganni ba. Kuma na san yasan na shigo ɗin rainin hankalinsa ne kawai. Kaina a ʙasa daga ʙofar ɗakin na furta, ā€œDan ALLAH ina son muyi maganaā€.
        Bai tanka min ba, bai kuma fasa abinda yake ba. Sai da ya mula dan kansa kusan minti biyu sannan ya magantu. Cikin silent voice ɗin nan tasa a daʙile ya furta, ā€œKi wuce wanka baʙi zasu shigoā€.
            Ji rainin hankali, ina masa wata maganar yana min wata. To ina ruwana da wasu baʙinsa. A zahiri kam sai na ʙara sauke murya har lokacin kan nawa a ʙasa. ā€œDan ALLAH kayi haʙuri ka barni naje can inda na saba. Ko kuma na koma sashen Ummie tunda dama a yanzu kusan acan ɗin nake. Ya Awwab taya zan dawo nan bayan kasan akwai matsala. Babu fa wanda yasan akwai wani maganar aure a tsakaninmu a gidan nan. Mi kake tunani zasu fassara zaman nawa?ā€.
           ā€œSu fassara duk yanda yay musu! Idan kuma kina buʙatar su sanin ne, yanzun nan sai na tarosu su saniā€.
        Da sauri na ɗago ina kallonsa. Yanda yay maganar kansa tsaye babu wani alamun ya ɗauki zancena da muhimmanci. Kai wlhy stubborn mutumin nan ya fara isata. Da ʙyar na iya dannewa muryata na ɗan rawa na ce, ā€œIdan kai zaka iya fuskantar su ka kuma ɗauka komai wlhy ni bazan iya ba. Sannan ba wannan rigimar nake so ba yanzu lafiyar Ummie ce damuwata. Dan ALLAH ka duba zance na yana da muhimmanciā€¦ā€
            ā€œKin dameni Madam wuce wanka kafin nazo kankiā€.
        Ya faɗa da ɗan kaushin harshe yana ajiye cumb ɗin hannunsa yana barin wajen. Karan farko naji hawaye sun gangaro min.
          ā€œKarna fito na sameki a wajenā€.
      Ya sake faɗa dai-dai yana shigewa cikin cikin closet ɗinsa. Hannuna na dunʙule kamar zan kaima bango naushi sai kuma na tausayama kaina dai. Dan nasan nice zan sha wahalar a ʙarshe hannunna ya rugurguje a banza. Hararar inda ya shige ɗin nayi ina cizar lips ɗina da ʙarfi, ga hawaye share-share a fuskata. Jin motsin kamar zai fito ya sani zabura na nufi bathroom ɗin. Dole ina ji ina gani na haɗa ruwan wankan nai ʙoʙarin fara yi. Wankan nake ina hawaye da hango irin bala’in da zai iya biyo baya. Dan wlhy abin bazai zama mai sauʙin ba a gareni. Gara sashen Ummie da nake zama shi wannan suna ganin ai kamar ina cutuwane shiyyasa aka ɗagamin ʙafa. Amma nan fa? Ni kaina idan an titsiyeni ban san mizan ce ba. Dan nayi alʙawarin in har bada kansa ya fito ya bayyana musu wacece ni ba wlhy ko za’a kasheni bazan faɗa ba. Sai da na kammala wankan sannan hankalina ya tashi, dan ban san yaya zanyi da kayan sakawa ba kuma. Bathrobe ɗin sa na ɗauka na saka. Sallar walha da nake son zuwa nayi dan lokacinta yayi ya sani haʙura na fito, amma sai da na leʙa cikin ɗakin sannan. Shiru babu motsin komai, sannan a iya hangena ban hango alamar akwai mutun ba. Ɗan ajiyar zuciya na sauke na fito a ɗan ɗarare. Nannauyar ajiyar zuciya na sauke ganin tabbacin baya ɗakin, tunanin sauri na shafa mai yazo min, dan haka na nufi gaban mirror ɗin nashi. Zama nayi tare da bin kayan dake akai da kallo, cikin ɗan taɓe baki na furta, ā€œSai kace maceā€. Da ʙyar na iya gane man shafawa, ina son na fara dubashi ina tsoron yin jinkirin da har zai dawo ya saman a wajen. Da sauri-sauri na shafa man da duk abinda zan iya amfani da shi a wajen. Na miʙe raina fal tashin hankalin kayan daya kamata ace na saka ya shigo. Daburcewa nayi dan abin yazo min a bazata. Rasa makamar riʙewa ta sani komawa kan stool ɗin kujerar na zauna tare da duʙar da kaina. Baiyi magana ba, sai madaidaicin akwati da yazo ya ajiye gab dani. Juyawa yay yayi ficewarsa yana faɗin, ā€œZanje wajensu, da munyi salla zasu shigo. Zaki iya zuwa duba Ummien kafinā€. Daga haka yay ficewarsa. Da kallo na bisa duk kaina duk a ɗaure. Sai dai furta zan iya zuwa duba Ummie ne yay matuʙar wanke min zuciya. Mikewa nai cike da zumuɗi harda daka tsalle dan farin ciki, tuni na nema damuwata da tunanin wasu baʙi da ya ishi mutane da zancensu na ɗauki akwatin daya ajiye ɗin. Saman gado na kaisa na buɗeā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’š’Šš’š’†š’•š’†š’†š’

    …….Kayane ɗinkakku har kala biyar, sai kayan ciki b&p 12-12. Sosai naji kunya ta kamani. Wani gefe na zuciyata kuma na mamakin inda yasan seize ɗina. Hatta da ɗinkunan dai-dai jikina cif. Zumuɗin tafiya wajen Ummie ya sani ajiye komai gefe na shirya cikin doguwar rigar lass pink mai ʙyau mara nauyi kuma. Komawa nayi gaban mirror ɗin ina kallon kaina fuskata cike da murmushi. Na dawo Samraah ta Ę“ar jarida Ę“ar gayu. A take yaya Musaddiq yazo min a rai. Hawaye naji sun cika min ido na kewarsu. Tunda abin nan ya faru bamuyi waya ba. Dolene idan na dawo wajen Ummie na roʙesa aron waya nayi kiransu har su aunty Zakiyya ma. Da wannan tunanin na ɗauki turarensa na fesa tare da ɗaukar ɗankwalin nai simple ɗauri. Mayafin cikin akwatin guda uku na ɗauka ɗaya nayi salla dan babu hujjab. Ina idarwa na miʙe cike da zumuɗi na tattare duk kayayyakin dana baza na maida bathrobe ɗin danai amfani da ita da towels ɗin daya cire na maida bayin. Sake ɗan gyara fuskata nayi da faran fauda ɗin dana gani sannan na fice.
         Nayi mamakin ganin falon ʙal yanzu yana zuba ʙamshi ga sanyin ac duk da dai ɗazun ma ba wani datti bane. Amma daga gani yanzu kasan an sake gyarashi. Kaina tsaye na fito batare da jin damuwar idan na haɗu da wani yaya zanyi ba. Koda na shiga sai da na sauke ajiyar zuciyar jin daɗin ganin babu kowa a falon. Dama ba lallai na samu masu aiki ba, dan yanzu lokacin hutu ne an gama na safe sai kuma azhar tayi. Kaina tsaye na haye sama harda ɗan guduna.

            Naji matuʙar farin cikin samun sashen Ummie fes da shi, ga ʙamshi na tashi tako ina. Da alama aikin Mama Balki ne kuwa. Ilai kuwa a ciki na sameta tana bama Ummie abinci. Da gudu na naje na faɗa jikin Ummie ina mai sakin kuka. Dariya Mama Balki ta sanya min, niko ko’a jikina murnar ganin Ummie kawai nakeyi. Sai da na gama murnata na ɗago ina kallonta. Itama kallona kawai takeyi kamar ta samu television. Murmushi na sakar mata idanuna cike da ʙwalla na ce, ā€œUmmie na i miss youā€.
          A bazatar da ta bamu matuʙar mamaki mukaga ta saki murmushi tare da kai hannu ta shafa kaina. Sai kuma ta saki kuka. Ruɗewa mukai mu duka. ʘoʙarin miʙewa nake a jikinta amma sai ta riʙeni da ʙyau, sai kawai na sake rungumeta nima ina kukan. Mun jima a haka kafin na ɗago jin kamar jikinta ya saki. Mama na kalla, ta sakar min murmushi itama tana share ʙwallar idonta. A raunane ta ce, ā€œTayi barci. Dan tasha maganinta bayan na gama bata abinci. Gani nayi ga sake jawo kwanon sai nayi zaton bata ʙoshi ba shine na sake zaman bata kika shigo.ā€
          Nawa hawayen nima na share. Sai kuma na tashi a jikinta muka taimaka mata ta kwanta. Zama nayi a kusa da ita hannunta cikin nawa ina jin matuʙar farin ciki da ganinta. Sai matuʙar tausayinta dake cimun rai da zuciya dan duk ta rame min a ido alamar ciwon ya bugeta sosai wannan karon…
      
    🩸🩸🩸🩸

        ā€œKamar ya an sallamesu? Waye ya sallame sun?ā€. Ta faɗa cikin daka tsawa. ʘanʙame jiki nurse ɗin tayi jikinta na rawa. Cike da tsorata da birkicewar Hajiya ʙaramar ta ce, ā€œAm sorry Maa. Wlhy ni ban san wanda ya sallamesu ba, naga kawai sun fito ne amma Dr Larai ce ta musu rakiya har mota. Muma ganin haka yasa muka rakasuā€.
             Wani irin tashi sama jijiyoyin Hajiya ʙarama sukayi, a fusace ta sake dakama Nurse ɗin tsawa. ā€œGet out of my side!!ā€.
        Ai da gudu Nurse ɗin ta fice kuwa. Har neman faɗuwa take, ALLAH dai ya taimaketa ta dafe bango. Tana fita itama Hajiya ʘarama ta fice a fusace. Sai da taje ʙofar office ɗin Dr Larai sai kuma ta gyara yanayinta cikin jan numfashi da saukewa. Knocking ʙofar tayi, aka bata iznin shiga. Dr Larai na zaune da waya a hannunta da alama akwai abinda take yi. Shigowar Hajiya ʙaramar ya sata ajiye wayar tana murmushi. Da girmamawa matsayin Hajiya ʙarama na shugaba a asibitin ta ce, ā€œWelcome Doctor ashe kin shigo? Yanzu nake tunanin zuwa na duba kafin na wuce gida ai damaā€.
         Murmushin yaʙe Hajiya ʙarama tayi, tare da jan kujera ta zauna. Hakan yasa itama Dr Larai komawa ta zauna. Gaisuwa sukai a mutunce. Kafin Hajiya ʙarama ta tambayi bataga petient ɗinta ba. Kota canja musu ɗaki ne?. Da ɗan mamaki Dr Larai ta ce, ā€œKunyi saɓani kenan? Dan sun wuce gida. Yaron nan naku rigimamme ne na bugawa a jarida. Dan har office ɗin nan yazo ta tirkeni sai na bama yarinyar nan sallama. Babu irin son fahimtar da shi ɗin da banyi ba dan ya barta ta ʙara samun sauʙi sosai amma fir yaʙi. Wai a dinga zuwa gida ana dubata. Ko kuma ya kawota asibitin kullum. Rikitaccen mutum ne na lura mai ra’ayin riʙau gaskiya.ā€
         Da ʙyar Hajiya ʙarama ta ʙaʙaro murmushi. Sai kuma ta miʙe tana faɗin, ā€œAi in dai Awwab ne ʙyaga da yawa wlhy. Shike nan bari zanje gidan mu haɗu ai.ā€
        Murmushi itama Dr Larai tayi da faɗin, ā€œTo shike nan hakan ma yayi, amma ina tausayama matarsa dan zata sha fama. Stubborn namiji irin wannan idan baka karancesa ba wahalar zamane da su. Dan su abinda  suke so kawai za’ayi tilas.ā€
            Murmushi kawai Hajiya ʙarama tayi dan ita abinda ya dameta shi ya dameta. Cikin wayancewa dai tace bara taje taga petient sun taru. Miʙewa itama Dr Larai tayi tana tattara kayanta. ā€œOkay nima ai wucewa zanyi. Nasan Alhaji bazai wuce ba sai na koma.ā€

        šŸ’¦šŸ©øšŸ’¦šŸ©øšŸ’¦

             Tuni ganin Ummie yasa na manta da dokarsa ta kar na daɗe. Na shagala sosai da kwance mata gashinta bayan nayi sallar azhar, kanta na a saman cinyata ʙamshin turarensa ya cika ɗakin. Da farko ban maida hankali ba saboda nasan na saka wani a jikina. Sai da naji alamun mutum na nufoni sannan na farga. Shi ɗinne dai sanye cikin brown wando da ash ɗin riga mai gajeren hannu. Gashin nan a ɗaure ta can ʙasa sosai dan har yana taɓa bayansa. Saukar iska a cikin idanuna ya sani jan numfashi da ʙarfi na lumshe idanun, sai kuma duk kunya ta kamani irin wannan abin kunya haka na kure bawan ALLAH da ido. A zatona zaiyi maganar kallon sai naji baice komai ba. Sai ma hannunsa da ya ɗaura saman nawa dake tsefe kan Ummie. A hankali na ɗan ɗago na kallesa. Shima ni ɗin yake kallo. ʘure juna mukai da ido ga hannayenmu akan Ummie. 
          ā€œKinga mamanki kin manta da umarni na ko?ā€.
       Ya faɗa a hankali kamar mai raɗa. Fuska na ɗan marairaice masa da karyar da kaina gefe a shagwaɓe na ce, ā€œKanta ne fa ya tsufaā€.
          Idanunsa ya ɗan ja luuu kamar zai lumshe sai kuma ya buɗesu tar akan nawa. Bazan iya jurar salon kallon nasa ba a yanzu dan haka na janye nawa a hankali na duʙar da kan. Shima sai bai sake cewa komai ba ya ɗan janye hannun nawa ya ʙarasa tsefema Ummien. Dama ɗayan da nake yinne ya rage. Dan bana mata kitson da yawa. Koda ya kammala cumb dake saman cinyata ya ɗauka ya taje mata kamar yanda naima sauran. Sannan ya tattare gashin cikin hannunsa. Kallona yay a hankali ya furta, ā€œCire band ɗin kaina, idan kin dawo kwayi kitsonā€.
         Kai kawai na jinjina masa. Kafin a kunyace na kai hannuna saman gashinsa dake kwance luff yana ʙyalli kona wata macen albarka na zame sililin baʙin band ɗin daya haɗe da gashin sai ma ka ʙura ido kake ganewa. Koda yaushe kuma zakaga da irinsa yake ɗaure gashinsa. Ina gama zarewa gashin nasa ya tarwatse a baya. Sai kawai na shagala da kallonsa har sai da naji saukar hannunsa cikin nawa zai zare band ɗin sannan na dawo hankalina. Duʙar da kaina nayi kunya duk ta isan. Yau dai na kula kamar ina sakin layi da yawa. Sai dai yanda ya basar yasa na ɗan ji nutsuwa. Yana gama ɗaure mata ya gyara mata kwanciya shima ya miʙe yana faɗin, ā€œLets goā€.
          Dole na mike a hankali ina gyara mayafin jikina. Wani kallo ya dinga bina da shi daga sama zuwa ʙasa. Sai kawai nai gaba da sauri. A falo muka samu mama Balki ashe bata fita ba. Tana ganinmu ta saki murmushi da faɗin, ā€œHar kun fito.ā€ a kunyace na jinjina mata kaina. Shi kuma ya sanar mata akwai baʙi a gidan zuwa anjima zai kira wayarta tazo su gaisa. Ya kuma roʙeta ta rufe ʙofar falon ko Paah ne yazo karta barsa ya shigo. Maganar tasa ta ɗan ban mamaki, har na kasa haʙuri sai da na kallesa. Amma sai ya ɗauke kansa kamar ma bashi ne yay maganar ba…

           A falon ʙasa muka ci karo da su Azizat. Tunda muka fara sakkowa duk suka miʙe tsaye tamkar waɗan da ke cikin shock. Dan su duka bakunansu a buɗe suke kallonmu idan ka cire wata farar budurwa da ban sani ba a gidan dake zaune ita bata tashi ba. Sai dai itama ta zuba masa ido kamar zata cinyesa. Kallo ɗaya na musu na ɗauke kaina. Kamar yanda shima naga baima nuna yasan da zamansu ba ya wucewarsa. Ina jiyo Malika na yin ashar a hankali. Ban san miya basu mamakin ba. Ganina a gidan? Ko kuwa ganina tare da shi?. Oho dai can ta matse musu. Dan ni su duka ukun a yanzu na shirya duk wadda tace zata shigo sabgata wlhy sai na mata zanen yarabawa a fuska.
           Koda muka iso ʙofar shiga sashen nasa sai da na tsaya na ɗan gyara mayafina sannan na bisa dan shi har ya riga ya shiga. Da Hayatu na fara cin karo tsaye a ʙofa yana waya, muna haɗa ido ya wani rissinar da kai. Harara na balla masa na wuce ciki abuna. Bana ganin fuskar waɗanda ke a zaune, sai dai haka kawai zuciyata ke wani irin sanyi da jikina. Gani nike kuma kamar na sansu. Tamkar wadda ʙwai ya fashema a ciki na ʙarasa sosai cikin tsakkiyar kujerun ina sake yin sallama ʙasa-ʙasa batare dana kallesu ba. Turus na tsaya zuciyata na bugawa da ʙarfi sakamakon jin muryoyin da ko’a cikin barci bazasu taɓa iya su ɓace min ba. Jikina har rawa yake na ɗago dan tabbatarwa. Sai kawai naci karo da fuskar Yaya Musaddiq da ke faman min murmushi da ta Hafizzullah. Yanzu kam sosai rawar jikina sake bayyana tayi, ga lips ɗina na rawa kamar yanda hannuna ke rawa ina son nunasu amma na kasa……..āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’˜š’†š’š’•š’š

    ……..

    ……Cikin rawar jiki na nufesu da wata irin sassarfa na faɗa jikin Yaya Musaddiq na saki wani irin kuka da ni kaina bamma san na minene ba, sai kuma na jawo hannun Hafizzullah shima na haɗasu na rungume. ā€œOh oh Kandala na ashe bata canja hali ba har yanzu jama’ar ALLAHā€. Yaya Musaddiq ya faɗa cike da tsokana yana ɗagoni a jikinsu. Cikin dariya da sharar hawaye Hafizzullah ya ce, ā€œALLAH Yaya bata canja ba sai ma abinda ya ʙaru.ā€ hannu nasa a kansa na dungure nima ina sharar hawayen na ce, ā€œMagulmaci kana nan da haliā€.
         Dariya muka sanya mu duka ukun. Kafin na sake kamo hannayensu cikin nawa su dukan. Cikin shagwaɓa na sake fashe musu da kuka ina faɗin, ā€œYa akai kuka zo nan? Waye ya kawoku? Yaya wlhy nayi kewarku, kullum da dare sai nayi kukan rashinku. Yaya dan ALLAH kuce kun dawo nan zaku zauna tare dani?ā€.
         Murmushi kawai yaya Musaddiq keyi, sai Hafizzullah ne cikin dariya ʙasa-ʙasa ya ce, ā€œSai dai idan zaki bimu mu koma Kano. Dan ni ban wani yarda kinyi kewarmu ba Addah. Jibeki kinyi wata fresh kamar ɗanyan nama sabon yanka. Ga ʙiba kin haɗa kamar ke kaɗai ake ma tirka a gidan. Kai gaskiya ba wani kewarmu ke dai gidan miji daɗi kinma manta da muā€.
             ā€œYaya ka ganshi yana tsokalana ko?ā€. Na faɗa a shagwaɓe batare dama nasan mi nake ba. Dan wlhy duk jina nake a ruɗe kamar a cikin mafarkin dana saba. Dana farka zan nemesu na rasa ne. A hankali Yaya Musaddiq dake murmushi har yanzu yana kallona kawai ya kai hannu ya share min hawayen yana faɗin, ā€œManta da shi, har kin manta da halin auta ne ma. Bayan da yaji zanzo badashi ba ya zauna ya dinga rusa kuka harda birgima a tsakar gida wai shi idan baizo yaga Addarsa ba zai faɗa rijiyan gidan su Mama Sadiq maʙotanmuā€.
           Dariya na ʙyalʙyale da shi, tare da kai hannu kan fuskar Hafizzullah daya kwaɓe ta cike da shagwaɓa naja kumatun, sai kuma na dunguresa da faɗin, ā€œAshe dai yaron nan na sona har yanzuā€ā€¦
     
         Duk abin nan dake faruwa yana zaune a falon. Binsu kawai yake da kallon ʙasan ido wani abu na masa motsi a zuciya. Daka gansu kaga waɗanda sukai matuʙar shaʙuwa da juna, suke kuma tsananin so da ʙaunar juna. Wani irin lumshe idanunsa yay murmushi na suɓuce masa a bazata. Hoton Fahad ne ya fara masa gizo a cikin idanunsa dake rufe, da sauri ya buɗesu yana cizar lips. Dan wani irin zafi zuciyarsa ta fara masa. ʘoʙarin ture tunanin dake neman kutso masa a zuciya yayi ya sake maida dubansa kansu. Hakan sai yay dai-dai da Samraah ta juyo suka haɗa ido kuwa. A mamakinsa sai ta sakar masa murmushin da har ya bayyana haʙwaranta. Sai ya samu kansa da lumshe idanun da buɗewa. A hankali ya furta, ā€œDama haka ake tarban baʙi da surutu?ā€.
             Murmushin ta sake sakar masa tana miʙewa daga durʙuson da tayi a gabansu. Muryarta kanta na nuna alamun farin ciki ta ce, ā€œYa Awwab ALLAH daɗine naji kamar ya kasheni. Ashe dama kasan yan gidanmu amma baka tafa faɗa min ba? Nagode, Nagode kaima ALLAH ya faranta maka fiye da yanda ka faranta minā€.
             Kansa ya ɗan girgiza yana sakin murmushin daya kasa riʙewa. Sai kuma ya maida kallonsa ga su Yaya Musaddiq da suma ke murmushin, muryarsa da alamun tausasawa ya furta, ā€œBara na ɗan je bazan jimaba zamu dawo. Please ku ʙara cin abinci sosai nan ɗin gidanku ne.ā€
        Faɗaɗa murmushin yaya Musaddiq yayi, cike da girmamawa ya ce, ā€œMun gode sosai ranka ya daɗe. ALLAH ya saka da alkairiā€.
           ā€œDon’t say me thanks you or ranka ya daɗe ɗin nan. You are my brothers. By now we are family ne okay. Nine zan kiraka Yaya, sai kuma small kiddo Hafiz a gefeā€.
         ā€œYes babban Yayaā€.
      Cewar Hafizzullah cike da farin ciki. Yayinda Yaya Musaddiq keta murmushi dan shi sake ganin al’amarin yake kamar a mafarkinsa. Duk da bayanin da Hayatu yay masa tare da Maash ɗin kafin shigowar Samraah zuciyarsa ta kasa daina mamakin komai. Cikin jinjina kai ya furta, ā€œNi ne ya kamata na kiraka Yaya, kaga dama ni kaɗaine banda Yaya. Yanzu kuma na samu. I am so happy inada wanda idan nayi ba daidai ba zai tsawatar min, inada wanda nima zan yima kuka a jiki. Ka mana komai na rayuwa. Daba dan kai ba da yanzu ban san a wane hali muke ba, dan in har wani abu zai taɓa rayuwan Samraah mu dukanmu tamu rayuwar zata girgiza ne. Saboda mu duka biyun itace rauninmu. ALLAH ya faranta maka fiye da yanda kai manaā€.
           Hayatu da Maash ɗin suka amsa da Amin. Dan gaba ɗaya ma Maash ɗin ya rasa abin faɗa. Idanu suka haɗa da Samraah dake kallonsa tana murmushi. Cikin ɗan ʙanʙance cat eyes ɗin nashi ya ɗage gira sama da ɗan ɗage kai alamar kallon fa.

         Samun kaina nayi da jin kunya, dan haka na duʙar da kan nawa kawai ina murmushi. Dan har ʙasan raina ban taɓa jin ya sakani a farin ciki irin na yau ba. Ji nake kamar naje na rungumesa. Amma ina jin kunya. Ɗagowa nayi na ɗan kalli Hayatu, shima a karo na farko na ce masa, ā€œThanks Youā€.
          Murmushi shima ya sakar min yana yin ʙasa da kansa. Sai kuma ya jinjina kansa da faɗin, ā€œNine zan gode ai Aunty naā€. Yanzu kam Harara na balla masa ina ɗauke kaina da murguɗa baki. Sai ko muka sake haɗa ido da ogan nasa. Ɗauke fuskata nayi gaba ɗaya daga sashensu. Sai da naji Hayatu nama su Yaya Musaddiq sallama akan sai sun dawo sannan…

        🌿🌿🌿🌿

           A hargitse Hajiya ʙarama ta koma office ɗinta. Kofar ta kulle dan bata buʙatar ganin kowa. Kai-kawo ta shiga yi cikin Safa da marwa. Kafin ta jawo waya ta shige cikin toilet. Sau uku tana kira amma ba’a ɗaga ba. Kanta ta dafe cike da takaici. Yanzu haka yana can yasha giyar tashi yana shaɓar barci. ā€œMotsowwā€ taja tsaki tare da fitowa. Wayar ta wurga saman desk ɗinta, itama ta zube a kujera tana mai dafe kai. Ji take yana wani irin sara mata. So take tai magana da wani ko zataji daɗi. Amma dawa ɗin zata yi. Da sauri ta sake rarumo wayar ta danna ma Jannifer kira. Bugu ɗaya kuwa ta ɗauka. Jin muryarta wani iri ta sata jan tsaki. ā€œMalama dalla koma dawa koke tare ta tashi taba mutane waje magana zamuyi.ā€
            ā€œBara dai ni in tashiā€.
        Jannifer ta faɗa tana Ę“ar shaʙiyar dariya. Tsaki kawai Hajiya ʙarama tayi batace komai ba. Sai da Jannifer ta sanar mata ta fito tana jinta sannan ta sake jan tsaki da fara magana. ā€œJannifer wai ina kika samo yarinyar nan ne? Wlhy tunanina gaba ɗaya nan birkicewa yake a wannan gaɓar?ā€.
           Da mamaki Jannifer ta ce, ā€œKamar ya? Wani abu ne ya sake faruwa?ā€.
        ā€œMiye ma bai faruba. Yanzu nan nazo asibiti na samu wai banzan yaron nan Awwab yazo ya ɗauke yarinyar nan sun wuce gida?ā€.
                ā€œTofa babbar magana. Wai Maash kike nufi?ā€.
        ā€œTo in ba shiba waye zaima mutane wannan gadaranā€.
    Dariya ce ta kufcema Jannifer, sai da tayi mai isarta kafin da ʙyar cikin dariyar ta ce, ā€œKai amma yaron nan ʙwallon shege ne wlhy. I like him style wlhy. Komansa yake baya tsoron uban kowa. Ya taka na waje kuma na gidan bai barku ba ciwon kan da gwale-gwale yake baku. To wai kodai son yarinyar nan yake ne? Abinfa da mamaki wlhy, dan ni bammaga wani damuwa a tattare da shi akan abinda ya aikata ɗin ba. Ka ɗirkama yarinya fyaɗe amma ka dinga abu It’s like you don’t care, I really like this boy’s style.ā€
          ā€œMtsowww!! Jannifer ban son shirme. Ina miki maganar serious kina mun wani soki burutsu.ā€
           ā€œEhm sorry Maa. ALLAH abunne ya ban dariya ya kuma burgeni. Samun irin stubborn mazan nan ba ko inaba. A Abuja nasan yarinyar ni gaskiyaā€¦ā€¦ā€ ta kwashe komai data sani akan Samraah ɗin tun daga haɗuwarsu da abinda ya faru kuma duk ta gaya mataā€.
         Cikin damuwa Hajiya ʙarama ta ce, ā€œAmma kema kinyi ganganci da baki san labarin nata baā€.
           ā€œTo banda abinki Hajjaju mizai sa na damu da labarinta. Ni fa dama irinta na fita nema. Sai kuma na samu miya rage min. Kaiwa na ɗako nazo na samu kuɗaɗena ai.ā€
        ā€œMtsoww!! Aikin kenan. To ita kuma Mashi’a ya akai ta zaɓi yarinyar? Bayan nasan idan kin kawo yara sai sunyi fin wata biyu ma kafin ki saida su. Musamman irinta ma ai baki badata a masu aiki?ā€.
           ā€œHummm ki bari kawai, wlhy kuɗaɗe kawai na gani. Dan an samu kuskure ne dana aika a kira min su ta biyosu. Nace ta koma Alaja Mashi’a ta ganta ta nace ita take so harda ninka min kuɗi. Ni kuma kawai naga bazan iya ba na sallama. Dan nasan ko ʙasar waje na kaita ba lallai na samu abinda na samun ba a wajenta. Kuma ina ma jin nauyin Alaja Mashi’a wlhy. Kin san dai ba wannan karon ne na farko dana fara samo mata masu aiki ba. Tunda kusan yaran gidankun nan duk a wajena aka amshesu mafi yawanci kuma itace ke zuwa da ɗauka musamman ma masu kula da Hajiya Babba.ā€
        Numfashi Hajiya ʙarama ta furzar, dan tasan gaskiyar zance Jannifer ke faɗa mata. Mashi’a tana kallon Jannifer ne kawai a mai kawo Ę“an aiki. Kuma zama ta iya cewa itace ta nuna mata gidanta a lokacin da take neman masu aiki da zata wuce da su can Germany, shine take faɗa mata gidan Jannifer ɗin. Tunda ta ɗauka wancan yaran biyu ta wuce da su taji daɗin zama da yaran sai yazam duk sanda ta shigo Nigeria takan ɗaukama Hajiya Babba masu kula da ita. Ko idan taji wasu nason masu aiki takan musu hanya. Da yake itama halin Maash ne da ita yanzu haka yaran data ɗauka su biyu duk sunyi karatu a can. Ɗaya a cikinsu ma ta kusa aure da ʙanin mijin ita Mashi’a ɗin. ʘaramin tsaki taja da ture batun Mashi’a ta koma wanda zai amfaneta. Amma ba komai, ita Awwab ɗin ma ya saukaʙa mata aiki, a gidan ma wasan zaifi armashi tunda yarinyar a sashen masu aiki take. Zata dakata ta dawo sashenta da kwana, ta nuna saboda abinda ya faru ta Ę“anta yarinyar. Zata nema mata makaranta  kawai a wata ʙasar daga haka shikenan ta gama samun cikar burina……….āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’˜š’†š’š’•š’š-š’š’š’†

    …..Suna gama ficewa cike da zumuɗi na maido hankalina kansu Yaya Musaddiq. ʘoʙarin zama nake Hafizzullah ya ce, ā€œWlhy ji nake kamar a mafarki. Wai aunty Samraah kece matar mutum kamar Maash. Ya ALLAH Maash fa. Wai dan ALLAH Adda yaya akai haka ta kasance? Kodai dama ke kin san wa kika aura? Dan wlhy duk da sun sanar mana komai yanzu kuma a gabana komai ta faru lokacin auren sai nake ganin kamar dama dai kuna son junan ku ne ke da shi.ā€
         Harararsa na ɗan yi, sai kuma na koma kusa da Yaya Musaddiq na zauna ina sauke ajiyar zuciya. ā€œYaya dan ALLAH mi sukace muku? Sannan dama kaima baka san shi bane?ā€.
            Murmushi sosai Yaya Musaddiq yayi yana kallona. Sai kuma ya jinjina kansa. ā€œSamraah wlhy har yanzu ni kaina ina a cikin yanayin da Hafizzullah ɗin yake ciki ne. Dan harga ALLAH ban taɓa sanin Maash ne mijinki ba, taya ma zan kawo hakan a raina to. Bama ni kaɗai ba, hatta su Abba babu wanda yasan wa kika aura. Koda aka ɗaukeni aiki a companynsa na amsa ne saboda dalilai uku. Na farko dai bazan iya bijirema umarnin ogana ba. Saboda yana treating ɗina like uba. Ko Abba dake ʙanin mahaifiyata muke a hannunsa tun bamu san kammu ba bana jin ya damu da tarbiyyata kamar yanda ogana ya tsaya a kaina. Hakan yasa babu abinda zai ce nayi a rayuwar nan naʙi yinsa sai dai ina na saɓama ALLAH ne ko cutar da wani. Wannan kam bazan masa biyayya ba. Na biyu maganar video ɗin nan. Na yarda zanyi aiki a companyn da tunanin ko zan fahimci wani abu dan na sanki da naci akan abu, komai tsahon lokaci da za’a ɗauka bazaki taɓa barin maganar video ɗin nan ba. Na uku amsar aikin kamar samun wata hanyar cigaban rayuwa ne yazo mana mu duka. Dan bamu da kowa sai junanmu. Dolene nayi aiki tuʙuru in har bana saɓama ALLAH bane domin cigaba da gina rayuwarmu. A lokacin da aka samu matsala game da aurenki, mahaifiyar Mansoor tazo har gida taci mutuncin su Abba akan ɗanta bazai taɓa ya aureki ba, su bazasu haɗa zuri’a da ke ba, idan kuma muka matsa zata iya ɗaukar kowane irin mataki dan ganin ta rabaki da ɗanta. Kin san Kawu Musa da zuciya, dan haka shima ya balbaleta, sai kawai ta ɗaga hannu ta maresa. Kafin ta sauke hannunta mukaji itama an sauke nata marin. Ta gigita sosai, haka muma da mamaki muke kallon bawan ALLAHn daya maretan. Mutum ne cikin shigar kamala harda gemunsa, maganganun daya gayama mahaifiyar Mansoor a lokacin sun matuʙar birgemu. Sai muka ji sauʙin yanda kalamanta suka ʙona mana rai dama kowa na wajen a take muma mukace ko Mansoor ne autan maza kin barsa har abada. An gama duk wannan rikici Maman Mansoor ta wuce bawan ALLAHn nan shima zai wuce Kawu Musa ya dakatar da shi. Godiya ya masa muma haka. A mamakin mu sai kawai muka ji ya fara jera masa tambaya. (Yaro munene sunanka?) Yace masa Muhammad. Anan kake? Yace masa eh to yana aiki anan amma asalinsa ba mazaunin nan ɗin bane. Kana da aure? Sai da yay jim kamar mai tunani kafin yace masa a’a. Kana shirin yi ne? Nan ma ya amsa masa da a’a. Iyayenka fa? Yace suna nan a raye. Sai mukaga kawai Kawu Musa yayi murmushi. Batare da wani tunani ba kawai ya ce (kowa ya shaida. Ni Musa a matsayin yayan Abdul-wahab na bama wannan bawan ALLAHn Muhammad auren ɗiyata Samraah. Ina fatan bazaka taɓa watsa min ʙasa a ido ba. Ina fatan zaka tabbatar min da ʙyautata maka zato da nake yi. Ina fatan zaka riʙeta amana bazaka taɓa cin amanata ba. Idan kuma har akwai matsala ka fito ka sanar min wlhy zan fahimceka. Nima kuma badan bana son Samraah na baka ita ba. Ba kuma dan na zubar mata da darajanta nayi hakan ba. Yarinyata mai ilimin addini ce dana zamani. Sannan ʙyaʙyʙyawace mai tarbiyya. Kaga dai ban sanka ba, ban san daga inda ka fito ba. Komai daya faru daga UBANGIJI ne ba daga mu ba. Dan abinda kayi yanzu yasa nake ji a raina ko daga ina ka fito kai ɗin mutumin kirki ne, dan ɗan halak shike kare martabar tsoho a duk inda yaga za’a yaga masa rigar mutunci.ā€
          ā€œWlhy Kandala ya matuʙar jimawa tsaye bai motsa ba a wajen. Har sai da Kawu Musa ya dafa shi da faɗin. Idan fa har kaga akwai matsala kada ka saka kanka a cikin damuwa. Mu duka dake nan babu wanda zai zargeka da rashin ʙyautawa har abada. Kuma mun ʙulla zumunci da kai kenan har abada. Murmushi yayi, sai kuma ya ɗan jinjina kai da roʙon a bashi wasu mintuna zaiyi waya. Kai tsaye Kawu Musa ya bashi dama. Tafiyarsa waya muka samu damar tattaunawa muma, Kawu Musa ya fahimtar damu dalilinsa na yanke hukuncin nan. Ni dai dan banda yanda zanyi ne bazan iya jayayya da su ba na amince. Hakama Hafizzullah atake yace shi dai dan ALLAH a barki. Amma sai Kawu Musa ya mana nasiha da nuna mana illar barinki ba’a ɗaura auren a ranar ba. Ya kuma ce mu cigaba da miki addu’a in sha ALLAHU sai kinci ribar wannan auren. Dawowarsa ta katse zancen mu. Ya tabbatar ma su Kawu ya amshi aure, sannan waliyyinsa na tafe in sha ALLAHU kafin lokaci yayi. Shima kuma zai je ya dawo. Badan muna da hope ɗin dawowar tasa ba muka barshi, amma abin mamaki na takaice miki sai gashi muna ʙoʙarin wucewa masallaci. Sunzo tare da babban malamin nan Sheikh Muhammad bin Khalipha Al-Hussain a matsayin waliyyinsa. Sai wannan Hayatu da suke tare yace ʙaninsa ne. Sheikh Muhammad dai ba ɓoyayyen mutum bane a garin Kano dama Nigeria baki ɗaya, dan haka duka damuwarmu da wani wasiwasi ya kau. Sheikh Muhammad ya tabbatar mana Muhammad tamkar ɗa yake a wajensa, kuma in sha ALLAHU bazamuyi kukan haɗa jini da shi ba. Idan ma muna tunanin wani abu mu cire, dan wata hikima ce ta UBANGIJI shigowarsa rayuwarmu. Bai kuma ɓoye masa komai game da abinda ya farun ba. Kawu Musa yafi kowa shiga a farin ciki. Dan haka a take aka ɗaura aurenku bayan idar da sallar juma’a, aka kuma kwaso kayanki da aka kai gidan Mansoor aka maida gidan daya bada matsayin nasa. Bayan an kaiki kuma sai aka samu akasin ciwo da kika shiga har ya taho dake Abuja, daga baya ya sanar mana kuna Lagos wajen iyayensa. Koda yaushe muna waya da shi, amma bai taɓa gaya min komai da ya shafeshi ba. Sai a yau da muka iso an kaimu masauki kawai naci karo da fuskarsa matsayin mijinki. Bayan kuma ni sai a gobe zan gansa matsayin ogana bayan munzo wajenki. Kin san kuwa ruɗanin dana shiga Samraah. Har kusan faduwa nayi sai da Hayatu ya rikeni. Bayan sun bani ruwa nasha mun zauna a ɗarare Hayatu ya min bayani komai tun daga batun ɗaukar video har zuwa kidnapping ɗinki da mahaifiyar Mansoor tasa akayi, da karɓarki da yayi a hannunta sanadin bincike da yayi saboda kuɗi da aka nema a hannunsa da sunanki har 500m. Bayan ya gano bake bace amfani kawai ake son yi da sunanki ya kuma gano anyi kidnapping ɗinki shine ya kubutar dake. Yaso amsar video ɗin a hannunki lokacin kodan gudun kada ki sake shiga wata matsalar sai kikaʙi bashi. Sai kawai ya haʙura ya sake ki akan zai cigaba da bibiyarki har sai ya amsa dan in ba haka ba yasan wataran wani zai iya sake yunkurin cutar dake a kansa in har akasan da shi. Ya tabbatar mana shi ya kubutar dake daga auren Mansoor ne saboda kawai yasan bazaki taɓa samun farin ciki ba dan mahaifiyarsa da ʙanwarta ya tabbatar da zasu iya aikata komai akanki, yanda kuma basu samu kudin nan ba kema bazaki samu yanda kike so ba. Ko ran daurin auren da yazo ya biyo mahaifiyar Mansoor ne cikin ɓadda kama dan ya tabbatar tayi abinda auren zai fasu amma sai kawai tai abinda ya sashi tilas bayyana kansa garemu alhalin shi beyi niyyar hakan ba. Sai kuma kawai Kawu Musa ya masa ʙyautarki. Yace bazai iya watsama tsohon kasa a ido ba saboda sun bashi tausayi, koba komai shine ya saka auren rugujewa, idan bai amsa ba ai ya sake raunanasu kema kuma an cutar dake shiyyasa kawai ya amince. Sai kuma gashi auren shima ya zame masa alkairi, dan ya ce mana yanzu kin tallafi rayuwar mahaifiyarsa dake fama da jiyya shekara da shekaru. Nagode Samraah, Nagode matuʙa da kikayi haʙuri kika amshi ʙaddararki da hannu biyu, Nagode da kika kasance ɗiya ta ʙwarai, Nagode da kika cigaba da riʙe tarbiyyar ki. Dan tabbas naga tsagwaron jin daɗi a fuskar Maash game da ʙyautatama Mahaifiyarsa. Na tabbatar da koda a baya ba soyayya ce ta haɗaku ba yanzu kam yana sonki. Yana ʙaunarki, dan wannan alkairin naki ne muma ya jawo mana alkairin. Yanzu na fahimci dama Maash yaje garejinmu kai tsaye ne domin kawai ya ɗaukeni aiki, dan sai yanzu nake sake tariyo yanda aka ɗaukeni aikin cikin sauʙi ake kuma mutuntani da girmamani sama da ma’aikata da yawa. Gashi har an turani karatu wata ʙasa. Samraah tabbas ke ɗin alkairi ce. Gaba ɗaya halayen iyayenmu kin kwashesu. Dama ance TSUTSAR NAMA ITAMA NAMA CE. tabbas na yarda da wannan batu na malam bahausheā€. Ya ʙare maganar yana share hawaye.
         Da gani har Hafiz muma kukan muke. Dan labarin ya matuʙar girgizani. Ashe haka abubuwa suka faru ni ban sani ba. Ashe mahaifiyar Mansoor ce tasa akai kidnapping ɗin a da farko. To amma tayaya akai hakan? Da sanin Mansoor ɗin kokuma? Idan bada saninsa ba taya akai tasan da videon nan? Shiyyasa ba’a son zargi, na daɗe ina zargin Maash akan ɓata min aure dan shi ya aureni ya cutar dani ya amshi video ashe abin duk ba haka bane ba. Kai jama’a, lallai masu iya magana sunyi gaskiya da sukace zato zunubi ne koda ya kasance gaskiya. Nagodema ALLAH da ban taɓa masa tambaya akan auren ba duk da nasha son yin hakan kwarjininsa da shakka na hanani. Sosai nake jin kimarsa na sake ʙaruwa a cikin zuciyata. Ashe shine ma ya kubutar da ni daga hannun mahaifiyar Mansoor. Kai ban taɓa zaton matar nan zata iya aikata irin wannan al’amarin ba. Wato mutum kai dai kawai gansa ka barsa yanda ALLAH yayisa, akan kuɗi baka iya banbance mutumin banza dana ʙwarai da wuri, dan sanin zuciya sai UBANGIJIN kawai……..āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’˜š’†š’š’•š’š-š’•š’˜š’

    ……Sai ʙarfe kusan uku mijin Baby ya iso gidan cikin ʙatuwar motar da ta sake haukace imanin su Mom. Sam ita bama damuwarta rabuwa da ɗiyar ba. Sai santin motar suke da sake kambama irin dukiyar mijin Babyn. Faɗa ma ta yarda akai baby iyayenta na Gwarzo su mata batayi ba. Sai sake shiryata da akai ciki wata alʙyabba mai ɗan karan ʙyau. Itako ido ʙemaʙayau ba ko ɗigon hawaye. Hasalima inda kwalliyarta batayi ba gyara abinta take ko tace a sake mata kaza bata son kaza. Su dai su Gwaggo Gudidi sunyi sororo suna kallon ikon ALLAH.
          Abba baya nan ya fita, dan baiyi zaton mijin Babyn zai iso a lokacin ba kasancewar yasha jira kafin azhar amma shiru. Sai Alhaji Jafaru babban ɗan Gwaggo Gudidi ya jashi suka tafi wata gaisuwa a gyaɗi-gyaɗi. Su Gwaggo Gudidi suna tunanin ai za’a jira Abban su dawo. Amma mi sai gani sukai an fito da amarya baby tana taku ɗai-ɗai ko irin rufe fuskar nan ta amare batai ba. Sai ma hirarsu suke da kakarta Umma suna dariya. Babu wanda aka kalla a cikinsu aka wuce da Baby ʙofar gida aka sakata a narʙeʙiyar motar da angon nata yazo a ciki. Abu mafi ban mamaki mijin ko kallonsu baiyi ba. Sai Mom ɗin da Umma ne suka gaisheshi yana amsawa cike da shan ʙamshi. Baki a washe Umma tace, ā€œALLAH ya tsare to Alhaji. ALLAH kuma yasa ku dawo lafiya da babbar tsaraba ta tattaɓa kunnena. Alhaji mu ya maganar tafiyarmu saudia ne?ā€.
            Duk maganar da Umma take harararta Baby keyi, miye na wani tabbayar zuwa makka dan zubar da mutunci. Badai shine da kansa yace ya biya musu ba ai sai tayi hakuri taga lokacin yayi baice suje ba ko. Shikam ma ɗan mannin rainin wayon hannu kawai ya ɗaga musu a taʙaice ya ce, ā€œA jira lokaciā€. Daga haka ya ɗauke kansa tare da bama drivern sa umarni ko kallon amaryar tasa baiyi ba. Driver kam umarnin ogansa ya cika. Ya tada mota abinsa yay reverse har yana neman taka su Mom dake tsaitsaye. Ai tuni mutane suka shiga faman jinjina kawunan mamaki. Ƴan anguwa suka guntsa kowa da abinda ya fassara al’amarin. Dan kuwa dai sunga sabon salon ɗaukar amarya ganin idonsu.
          Duk abinda ake Halime batama sani ba. Tana can tunda ta idar da sallar azhar ta kira Abba tace ya saya mata rake da gyaɗa tai kwanciyarta. Har aka tafi da Babyn kuma bata sani ba. Sai da hayaniya ta fara tashi ta Ę“an gwarzo sannan ta farka…
       
    šŸ’¦šŸŒŸšŸ’¦šŸŒŸšŸ’¦

        Duk yanda Hayatu ke ʙoʙarin danne abinda ke cimasa zuciya ya kasa. Sai satar kallonsa yake ta cikin mirror har suka iso babban companyn da Ummie ta fara ginawa da hannunta tun mahaifinta na da rai wanda Paah ne ke riʙe da ragamar komai na companyn. ʘatone bana wasa ba, sannan akwai ma’aikata jingim a cikinsa. A farkon ginashi ana sarrafa kayan suturu ne, bayan abubuwa sun kwaɓe akan ciwon Ummie companyn ya durʙushe harma ya daina aiki na tsawon shekaru. Sai daga baya Maash ɗin ya farfaɗo da shi tare da sake faɗaɗashi aka maida shi wajen sarrafa kayan abinci. Kusan kowane nau’i na kayan abinci har su mai magi duk companyn na fitarwa. Suga, gishiri, harsu omo da sabulai sannan kayan abinci tun daga kan shinkafa, taliya, fulawa, garin alkama, da ire-irensu, da dangoginsu. A yanzu dai a Africa babu companyn dake fidda kayan masarufi irinsa gaskiya. Dan tako ina suna kai abinci kuma sunada wasu reshika a wasu kasashen da dama.
         Duk ta inda suka gitta gaisuwar girmamawa ake bama Maash. Shi ko yana mai amsa musu a daʙilen nan nasa dan motsin lips ɗinsa kawai suke gani sai kuma hannu da yake ɗaga musu. Duk wanda yayma Maash farin sani a rayuwa yasan wannan halin nasa ba wulaʙanci bane yanayinsa ne kawai a haka. Dan magana inba ta zamar masa dole ba, da wahala kaga yana yinta. Idan ma yayin bazaka taɓa jin sautin muryarsa sama ba. Sai fa idan an ɓata masa rai yayi matuʙar iya hargagin da ke gigita mutum.  
         Kai tsaye office ɗinsa ya nufa Hayatu biye da shi dan shima yana da office a companyn. Har yanzu suna kan bincike game da case ɗin nan na samun yara a containers ɗin sa na kaya da suka tura Ghana. Monday ɗin nan zasu shiga court yau kuma zai sake zaman meeting da lawyers ɗin su da Paah, duk da dai kwata-kwata an nuna case ɗin bai shafesa ba duk da kasancewarsa shugaban companyn shiyyasa ma yake tsula tsiyarsa da matan da ake ɗauka aiki a ciki har Maash ɗin ya gano sa ranar yake tujara. Sun samu Paah ɗin baya nan, lawyers ɗin kuma basu kai ga ʙarasowa ba. Sai hakan ya bama Hayatu damar fidda abinda ke ransa.
         Kallon Maash dake zaune cikin kujerarsa ta office ɗin yana daʙilar keyboard ɗin computer ɗin saman desk ɗinsa yayi. Sai kuma yayi ʙasa da kansa cikin girmamawa yace, ā€œYaya kamin afuwa, zan sake maimaita maganar nan dai ta kwanaki dana taɓa maka kaʙi cewa komaiā€.
         Shiru kamar maash ɗin bazai amsa ba. Sai kuma can yace, ā€œUhumm ina jinkaā€.
         Kai hayatu ya ɗan sosa yana sake ʙasa da kansa ya ce, ā€œNifa ALLAH yaya yau saina sake ganin kamanin Yayan Aunty sosai da Baba Abdull sun sake fitowa. Shi kuma ʙanin nan nasu Hafizzullah banbancinsa da Falaq kawai ita mace shi namiji. ALLAH tun ɗazu a ruɗe nake dauriya kawai nake yi. Ita kanta Auntyn yau sai naga suna fisgar kama da Falaq ɗin, kawai dan ita farace ita kuma aunty bata kaita hasā€¦ā€¦ā€
          Ruff bakin Hayatu ya rufe batare daya ʙarasa faɗa ba saboda kallon da Maash ɗin yay masa. Sai ya wayance da faɗin, ā€œYaya ALLAH ka duba lamarin nan iya gaskiyata nake faɗaā€. Ya ʙare maganar cikin shagwaɓa kamar ba Hayatu PA ba. (Wato na lura akwai lokacin da Maash matsayin oga yake a wajensa. Akwai kuma lokacin da yaya yakešŸ˜€).
          Hararsa kawai Maash ɗin yayi ya ɗauke kansa ya maida ga aikinsa….
      
    🩸🩸🩸🩸

             ā€œBan gane mi kike son faɗa ba? Kin san dai bana son rainin wayo koā€.
         ā€œWlhy yallaɓai babu rainin wayo a maganata. Kai ma kasan bazan yi hakan a gareka ba. Naje na samu nima ta sallameta. Kuma shi Awwab ɗin ne yaje ya sakata yin hakanā€.
         Wata shegen ashariya Yallaɓai ya kutuntuma. Sai kuma ya miʙe zaram yana kaima Centre table duka har sai da Hajiya ʙarama ta zabura tana ʙanʙame jikinta. Sai kuma ya juyi a fusace yana nunata da yatsa. ā€œIdan har na samu matsala a aikina saboda ke na rantse da ALLAH sai na koya miki hankaliā€.
             Sosai hankalinta ya tashi, dan tasan mugun nan komai zai iya aikatawa akan buʙatarsa. Amma ba komai lokacinsa ne. Zata bisa yanda yake so gaba kaɗan zatayi maganinsa ai itama. Dan ta gama shirinta a kansa tun shekarun baya. Murya ta sauke cikin nuna tsorata ta furta, ā€œKayi haʙuri nayi kuskure, amma na samo hanyar gyara kuskuren nawa. Na tabbatar bazai kaita ko’ina ba sai gida. Koda yake nama bincika an tabbatar min suna gidan. A wannan karon zan nuna abinda ya faru ina jin tausayinta na dawo da ita sashena. Kokuma na nuna zan share mata kukanta akan abinda ya faru ta hanyar nema mata makaranta ta cigaba. Da ganan sai musan abinda ya dace, kaga munma samu sauʙiā€.
         Shiru ya ɗan yi alamar nazarin maganarta. Sai kuma ya kai zaune yana mai jinjina kai. ā€œHakan ma yayi, sai dai ina mai gargaɗarki ki kiyaye. Dan bana buʙatar wata matsala kuma.ā€
           ā€œIn sha ALLAHU babu abinda zai faru, shi mai bincike a kantan ya dawo ne?ā€.
          ā€œZuwa jibi ne ʙarshen kwanakin daya ɗiba min. Dan ko jiya munyi waya da shi ya kuma tabbatar min da aikin na tafiya yanda zanyi farin cikiā€.
         Itama murmushin ta saki duk da ba haka taso ba. Dan a nata ɓangaren tasa itama a bincika mata wacece Samraah ɗin?.

           ✨✨✨✨

      Gaba ɗaya ganin Ę“an uwana ya wanke min duk wata damuwata. Hirarmu muke cike da farin ciki suna bani labarin cakwakiyar gidan Abba ta yanzu da amaryarsa, tare da yanda auren Baby ya kasance, sun dai baro ana jiran miji yazo ya ɗauke ta. Matsama Yaya Musaddiq nai ya kiramun aunty Zakiyya. Daga nan fa mukaita gaisawa da mutane harda amaryar Abba da kawai naji matuʙar ʙaunarta. Daga ʙarshe jikina yayi sanyi jin batun zuwan mijin Baby yanzu babu jimawa da yanda tafiyar ta kasance. Mun cigaba da jimanta abun bayan katse wayar. A haka lokacin sallar la’asar ya riskemu. Ina tunanin yanda zasu fita salla sai ga guard ɗinsa yazo yace suzo boss yace ya kaisu suyi salla. Kafin su dawo nima nayi tawa, na sake gyara sashen naje kuma na gano Ummie. Alokacin nake cema Mama Balki tazo su gaisa da bakin da yace. Ta ce tana zuwa idan ta kammala abinda take yi. Harta bani abinci na kai musu. Duk da sunci sun ʙoshi dan acan inda aka fara saukesu sunce sunci abinci, nan ma kuma da Hayatu ya rakosu da kayayyakin ciye-ciye suma mukaita ci muna hira sai da na ɗauka musu abincin. Sake zaman hirar mukayi, dan ji nake kamar mu dawwama a haka. Koda suɓutar baki ban sanar musu komai daya shafi gidan nan ba. Hirar abinda ya shafemu kawai mukeyi hankalinmu kwance. Hatta zancen alaʙar Mama Balki da nake zargi da baba ban gaya musu ba, shiyyasa ma na matsu tazo su gaisa. Dan duk wanda yasan mahaifinmu ya kallai Yaya Musaddiq yasan suna matuʙar kama, musamman yanzu da yake sake girma kamanin na sake fitowa sosai. Wajen ʙarfe biyar ina shirin zuwa na sake ganin Ummie da ga nan nayi kiran Mama sai gashi ya dawo. Sannu da zuwa su Yaya suka shiga yimasa da gaidashi. Ganin haka yasa nima na gaisheshi batare dana yarda na kallesa ba. Sai dai shi ina jin idanunsa na yawo a jikina, dan haka ma naʙi kallon nasa. Ciki ya shige yana faɗa musu bari ya ɗan watsa ruwa. Sukai masa fatan fitowa lafiya. Na gyara zama zan cigaba da hirata Yaya Musaddiq ya hararen, tare da mun nuni da ʙofar da ya bi.
            Baki na tura cikin shagwaɓa nace, ā€œKai yaya mi kuma zanyiā€.
        Sosai yake kallona fuska a tsuke, ā€œOh kice karatun Mom kema kin ɗauka kenan?ā€.
           Da sauri na shiga girgiza masa kaina. ā€œWlhy Yaya a’aā€.
        ā€œInafa a’a tunda gashi na gani da idona. Abba yakan dawo gida bai ishi Mom kallo ba. Kema ga mijinki ya dawo ko kallon inda yake bakiyi ba. Abba yakan dawo gida Mom bata bashi ruwa ba, ya shige yay hidimarsa. Kema kuma gashi mijinki ya dawo babu ruwa babu abinci, maimakon ki bishi kiji yaya ya dawo, miye matsalarsa kin gyara zama ke ga mai Ę“an uwa sunzo ko. Haka kike so muma idan munyi aure matanmu suna mana?ā€.
         Da sauri na sake girgiza masa kai idanuna na cika da ʙwalla. Ya ce, ā€œOkay to aya maza tashi, haba Kandalata ina islamiyyan ya tafi? Mu kin bamu munci mun ʙoshi yan uwanki shi dake wahalar nema ko oho. Ko kina so Hafiz ya rainakiā€.
            Da sauri na sake girgiza kaina ina Hararan Hafiz ɗin dake kumshe dariya. Tashi nayi na nufi ʙaton freight ɗin dining room. Ruwa na ɗauka da lemo na sa a tray dana ɗakko a kitchen sai glass cup mai ʙyau. Ni sai ma naji abun banbara ʙwai wai namiji da suna Hajara. Haka dai na daure dan bazan taɓa iya bijirema Yaya Musaddiq ba…….āœļø

    🄱A fito lahiya matar yayanmu.

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’˜š’†š’š’•š’š-š’•š’‰š’“š’†š’†

    =========

    …….A hankali nake tafiya kamar kazar da ʙwai ya fashema a ciki, koda na isa ʙofar bedroom ɗin na yi kusan minti ɗaya kafin nayi knocking a hankali. Banji motsin komai ba balle na saka ran za’a buɗe min. Hannu na kai zan sake knocking ɗin aka buɗe ʙofar. Da sauri na janye hannun nawa na riʙe tray ɗin da ʙyau kaina a ʙasa. Jin shiru ya sani ɗagowa a tunanina juyawa yay ya koma. Amma sai na gansa tsaye kawai ya zuba min cat eyes ɗin nan nasa. Sosai tsigar jikina ta tashi, dan wani irin kallo yake min mai wahalar fassara gashi da ga shi sai guntun towel iya gwiwa. Kaina nai ʙoʙarin sake saukewa cikin ɗan rawar harshe na furta, ā€œD… dama ruwa neā€¦ā€
          Bai bari na ʙarasa ba ya matsa min hanya alamar na shiga. Raɓawa nayi na wuce, kai tsaye na ajiye tray ɗin saman Centre table na buɗe ruwan na tsiyaya a cup tare da ʙoʙarin ɗagowa. Ido muka haɗa da shi, yana tsaye jikin mirror ʙafafunsa a harɗe yay folding hannayensa a ʙirji ya zuba min ido kawai. ʘasa nayi da nawa, tare da takawa a hankali inda yake, batare dana kallesa ba na miʙa masa kofin ruwan. Shiru babu alamar zai amsa, dan haka na ɗago cikin yanayin kamar mai shakku na kallesa, har lokacin idanunsa a kaina suke, samun kaina nayi da marairaice face ɗina kamar zanyi kuka na ce, ā€œPleaseeee!ā€.
            Ɗan luuuu yayi da idanunsa kamar zai lumshe sai kuma ya buɗe a kaina har sai da naji tsigar jikina ta tashi, hannuna dake riʙe da kofin ya ɗan fara rawa-rawa kamar zan saki kofin. Hannayensa dake harɗe a ʙirjinsa ya warware a kasalance, dan haka na ʙara ʙasa da kaina dan bazan iya kallonsa a yanda yaken ba. Jin saukar hannunsa a saman nawa mai riʙe da kofin ruwan ya sani lumshe nawa idon batare dana ɗago na kallesan ba. Ina ʙoʙarin sakar masa amma ya hana hakan, sai ma saukar ɗayan hannun nasa naji akan gefen cikina, a hankali ya fara tafiya da shi har zuwa bayana, kafin ya matsoni ya manne da jikinsa. Sannan ya kai ruwan da ke a cikin hannayenmu saman lips ɗinsa. Yasha kusan rabi ya zare kofin ya ajiye. Ni dai har lokacin ban sake yarda na kallesa ba. Sai dai na furta, ā€œNagode sosai Ya Awwab. ALLAH ya saka da alkairi, ya bama Ummie lafiya da tsohon rai mai albarka. ALLAH ya kareka da sharrin masu sharri. ALLAH ya yarda dakaiā€.
          Jinai kawai ya ɗora ɗayan hannun nasa ta saman bayana shima ya mannoni da jikinsa gaba ɗaya ya kwantar da kaina a saman faffaɗan ʙirjinsa. Luff nayi ina mai shaʙar narkakken ʙamshinsa mai matukar tasiri da saka nutsuwa a zuciyar mai shaʙa. Munfi mintina biyar a hakan har wani bacci-bacci nake ji yana neman ɗaukata. Sai naji ya ɗagoni a slowly tare da juyamu na koma jikin mirror ɗin shi kuma ya koma inda nake da. Dagowa nai da nufin yin magana ya ranʙwafo ni gaba ɗayansa, daɓas na koma saman mirror ɗin na zauna, shi kuma yamun rumfa hannunsa ɗaya dafe da mirror ɗin, ɗayan kuma ya saukesa akan haɓata ya ɗago fuskata. Cikin matuʙar low voice ya furta, ā€œOpen your eyesā€.
        Jinai Sam bazan iya masa gardama ba, dan haka na shiga yin far-far da idanun kafin na buɗesu da ʙyar na saukesu akan ʙyaʙyʙyawar doguwar fuskarsa dake ʙawace da kwantaccen gashi baʙi siɗik. Kallon juna muke cikin ido da mu kammu bazamu iya fassara yanayin da muke a ciki ba. Sai wani irin tashi tsigar jikina keyi, a hankali a hankali idanuna suka fara tara ʙwalla. Kasa jurewa nayi na lumshesu slowly ina sauke tagwayen ajiyar zuciya. Dan mutumin nan zai kasheni da salonsa. A bazata matuʙar bazata naji saukar abu mai sanyi da taushi saman lips ɗina. Da sauri na buɗe idanuna. Ai babu shiri na maida su da gudu na kulle zuciyata na tsargawa. A salon da yake kissing ɗin nawa yasa gaba ɗaya jikina ya saki har ban san na kai hannuna saman kansa ba nariʙosa. Har ga ALLAH hakan da nayi kawai nayi ne amma bada wata manufa bane, tsabar na rasa ina zan dafa na samu sassaucin ruɗanin dana shiga ne yasa hannuna sauka a saman kan nashi batare dana shiryama hakan ba. Ashe shi hakan armashi ya ʙara masa, dan wajen kicin-kicin ganin na janyesa harda zame band ɗin dake ɗaure da gashinsa na tura yatsuna duk biyar cikin gashin ina yamutsawa. Munfi mintuna uku a haka, kafin ya janye lips ɗin nasa tare da ɗaura goshinsa saman nawa, hancinanmu na gogar juna, kowannenmu na sauke numfashi. Wajen minti ɗaya sannan ya ɗago kansa, kasa kallonsa nayi, sai ma hawayen da suka cika min idone suka ɗan silalo badan ni kaina nasan dalilina nayin su ba, gaba ɗayana ya jawo ya rungume tsam-tsam a jikinsa. Nima samun kaina nayi da ʙanʙamesan dan jikina rawa yake yi.. nan ma mun kwashe wasu mintuna biyun a haka kafin ya kai bakinsa saitin kunnena cikin raɗa ya furta, ā€œKema baʙi ʙoshi ba ko? A ʙaraā€.
             Ji nai kamar na tsaga jikinsa na shige dan kunya, sai kawai na sake ʙanʙamesa. Wani irin ratsa kunnena sassanyan sautin murmushinsa yayi a bazata. Sai kuma ya ɗagoni yana ʙoʙarin kallon fuskata amma naʙi yarda yay hakan….

        A dai-dai lokacin da acan Maash da Sam-G ke a wata duniya anan falo Mama Balki ce ta iso domin gaishe da baʙi. Cikin fara’arta da kazar-kazar ta shigo bakinta ɗauke da sallama. Amsawa su Musaddiq sukayi dama ransu fal tunanin ganin wannan uba-uban ʙaton gida amma basuga giccin kowa ba sai masu aiki maza. Ɗagowa sukayi su duka a tare da nufin gaisheta, kawai saita ja birki da uban sauri har tana buge ʙafa da kujera. Kallon Musaddiq take kamar zata cinyesa da idanunta, jikinta sai rawa yake yi. Sai kuma ta sake maida kallonta ga Hafizzullah shima. Sai kawai gani sukai ta fashe da wani irin kuka tana faman jan jikinta baya.
          A ruɗe duk suka miʙe suna tambayarta lafiya? Mike faruwa?. Sam ta gagara basu amsa, sai sake cin tuntuɓe da tayi da carpet hakan yasata tafiya gaba ɗayanta zata faɗi ta baya suka hau salati da nufarta su duka biyun suka tare a tare….

           Cak Maash ya dakata daga yunʙurin sake maida lips ɗinsa da yake saman na Samraah. Itama sai ta buɗe nata idanun da sauri duk suka kalla ʙofar. Dan su dukansu sunji salatin su Hafizzullah ɗin Kasancewar da ʙarfi sukayi. Kallonta yay, itama ta kallesa, sai kuma a hankali ya zame hannayensa da ga jikinta ya ɗaga gaba ɗayanta ya sauke daga saman mirror ɗin daya ɗaurata.
        Zan nufi ʙofa da sauri ya riʙoni, fuska na marairaice masa kamar zanyi kuka. Sai yay min nuni da gyalena da ɗan kwali dake yashe a ʙasa. Gyalen kawai na ɗauka dan hankalina ya tashi, kada wani ya cutar min Ę“an uwafa a gidan nan? Da wlhy sunga ainahin baʙin halina dan saina gallabi kowa da kowa har uban gayyar tasu bazan bari ba. Dai-dai ina isowa falon suke ʙoʙarin zaunar da Mama Balki a kujera, sai nai turus ina kallonsu. Ruwa Yaya Musaddiq ya bata, yayinda Hafizzullah daya juyo ya ganni yake sanar min abinda ya faru. Da sauri na nufi Mama Balki. Zama nayi a kusa da ita cikin damuwa ina tambayarta mike faruwa?. Dai-dai nan ya fito shima sanye cikin baʙar jallabiya da tai masa wani masifar ʙyau. Muna haɗa ido na kauda nawa da sauri.
          Mama dake kallonsa itama fuskarta share-share da hawaye ta nuna masa Yaya Musaddiq. ā€œAlhaji ʙarami dan ALLAH kalla bawan ALLAHn nan. Kalla yanda yake tsananin kama da Babanku. Inda ace mutum na mutuwa ya dawo da ʙuruciyarsa babu abinda zai sa bazan dage Abdul-wahab bane ya dawo Alhaji ʘaramiā€.
          Shiru kamar bazaice mata komai ba, sai kuma ya ɗan nisa a hankali tare da kaiwa zaune cikin kujerar dake facing ɗinta. Zaman ʙafa ɗaya kan ɗaya yay yana mai kwantar da kansa a jikin kujera tare da lumshe idanunsa. A haka ya furta, ā€œPlease Mama relax. Wannan ba Baba bane, dan Baba ya tafi ya barmu tafiya ta har abada.ā€ ɗagowa yay da kansa ya ɗan zuba mana idanu mu duka sai kuma ya sake furzar da iska kaɗan yana ɗan mana nuni da Mama Balki. ā€œWannan matsayin uwa take garemu mu duka. Ban sani ba ko kun san Baba yana da mata a zamansa na Lagos harda yarinya ɗaya. Itace wannanā€.
           Da sauri Yaya Musaddiq ya kalla Mama, sai kuma ya juya ya kalla Maash ɗin. Sake gyaɗa masa kai yay cikin lumshe idanunsa tabbacin haka ɗin ne. Ni ko da Hafizzullah a ruɗani muke kallonsu. Gwarama ni dama na jima da wannan al’amarin a zuciya. Sai kawai mukaga Yaya Musaddiq ya duʙar da kansa yana hawaye. Kafin ya miʙe a hankali yaje gaban mama Balki ya tsugunna. Hannunta ya kamo cikin nasa hawaye na cigaba da masa gudu a fuska ya furta, ā€œALLAH na gode maka daka saka inada rabon ganin wannan rana kafin nabar duniya. Mama dan ALLAH kiyi haʙuri, kiyi haʙuri kiyi haʙuri. Tun daga randa nasan kaina, tare da labarinki a wajen Gwaggo Gudidi ban taɓa fashin addu’ar ALLAH yasa kafin nabar duniya na haɗu da ke da Ę“ar uwarmu da akace tana tare dake ba. A dalilinki sau biyu ina zuwa Lagos bayan na tuhumi iyayena akan kuskuren da sukayi suka nuna min nadamarsu suma, sai dai dan basu san ina zasu ganoki ba suma shiyyasa suka cigaba da zama da damuwar a rayukansu. Tabbas mama an cutar dake. Muma kuma an cutar damu, tunda da mun sanki na tabbatar bazamuyi kukan rashin iyaye a duniya ba. Dan ALLAH mama kiyi haʙuri ki yafema ahalinmu kada hakkinki ya cigaba da hanasu kwanciyar hankali a rayuwarsu. Kuskure ne sukayi a wata gaɓar da mu kammu bamu tsira ba. Dan mu ɗin ma komai sai da ya ʙwaɓe tsawon shekaru tsakaninmu dasu babu wani jituwa sakamakon amsata da ʙanin mahaifiyar mu yayi ya riʙe bai bar musu ba, duk da dama tun raduwar mahaifiyarmu ita Samraah da Hafizzullah suna a hannunsa ne. To nima sai yace zan koma hannunsa, amma suka nuna basu amince ba suma su Samraah sai a dawo musu da su. Kowa ya fahimci gadon da aka barmana sukemawa shiyyasa dangin mahaifiyarmu suka dage shine akai rabuwar tashin hankali suka manta damu sai da ga baya naita bibiyarsu har komai ya dai-daita. Zamma iya cemiki dawowarsu garemu sosai-sosai lokacin amsar kuɗin auren Samraah neā€. Kuka yaci ʙarfinsaā€¦ā€¦ā€¦āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    TypingšŸ“²

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›
    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†
    š‘·š’‚š’ˆš’† š’•š’˜š’†š’š’•š’š-š’‡š’š’–š’“

    ……Muma kukan muke ni da Hafiz sosai. Hakama Mama kuka take har tana siʙewa. Sai da ya mana magana cikin gyaran murya sannan kowa ya ɗan tsagaita. Cikin yanayinsan nan na rashin son hayaniya ya furta, ā€œKuka ba shine alama ta godiyar ALLAH ba. Abinda ya faru ya riga ya faru, ku fuskanci wanda yake a yanzu itace rayuwa. Ya kamata bayan magrib itama Falaq kuje can dan ta ganku tunda tana fama da kanta bazata iya tazo nan ba. Gashi babu wani lokaci shi Musaddiq zai wuce gobe in sha ALLAHUā€.
           Duk mun gamsu da zancensa, yayinda Mama ke jinjina kai ta ce, ā€œAlhaji ʘarami dama kasan inda suke kenan? Shiyyasa ka auro Samraah?ā€.
           Ɗan luuu yay da idanunsa kamar abin dole ya saki murmushi. Babu wanda ma yay zaton zai amsa a cikinmu saboda yanda ya jima baice komai ba. Sai kuma ya ɗan furzar da iska cikin sauke numfashi. Kansa ya girgiza a daʙile ya furta, ā€œA farkon ganina da ita ban san ita wacece ba. Ban kuma taɓa kawo wani abu game da ita ba. Sai dai sunanta ya ɗan so ya ja hankalina har ya tunamin da Baba a ranar. Abubuwa ne da yawa suka faru da suka alaʙanta wannan auren Mama, dan har ga ALLAH ni banje da nufin ɓata mata aure ni na aureta ba. Kawai na hana wancan ne dan na kuɓutar da ita daga halin banza na mahaifiyarsa. Sai kuma Uncle nata yace ya bani, naso kawo musu wani dalili sai kawai naci karo da fuskar Musaddiq nima a lokacin, shine kawai nace na amsa. Bayan barina wajen kafin a ɗaura auren na saka akamin bincike shine na gano su ɗin yaran Baba neā€.
            Sosai kowannenmu ke jinjina iko da hikima ta UBANGIJI. Hafizzullah da bai fahimci komai ba a zancen yay tambaya. Nice na masa bayani. Sai kawai ya hau murna wai muma ashe munada Mama. Abinda yay ɗin ne ya sakamu darawa mu duka. Hatta shi uban gayyar ina kallon sanda yay ɗan munafukin murmushin nan nasa dai-dai yana miʙewa. Ciki ya koma ya barmu anan da Mama. Aiko sai labari ya ɓalle a tsakaninmu, dan Mama wayayyar mace ce mai kuma tsananin kirki da dattako. Fita tayi sai gata tazo da Malam Baba. Mahaifin Hayatu kenan, mijinta kuma a yanzu, aminin mahaifinmu. Shi kansa ya shiga mamaki matuʙa, ya kuma yi farin ciki da ganin Ę“aĘ“an amininsa. Duk da ya jima zuciyarsa na masa wasi-wasi a kaina ashe. Shiyyasa tun ranar farko daya ganni agidan yake kallona. Dan duk da bana kama da Babanmu, gaba ɗaya komaina na mahaifiyarmu ne idan ka cire ɗan duhun da nake da shi dan mahaifiyarmu farace tass, su su yaya Musaddiq duk sun ɗakko farinta amma kamanin Baba. Maganar aure kuma dake a tsakanina da Maash ya sani Hayatu ya faɗa masu dama.
        
         🌺🌺🌺🌺

      Ganin har gab da magriba bai sake fitowa ba munata hirarmu da Mama a falo Yaya Musaddiq yay min nuni da hanyar bedroom ɗinsa cikin hikima. Jinai duk kunya ta gama kamani, sai dai bazan iya musa masa ba. Dan haka na tashi sum-sum na wuce. Yanzun kam ban tsaya knocking ba na murɗa handle ɗin ʙofar a hankali na shiga kaina a ʙasa. Dan har yanzu ina jin nauyi da kunyar abinda ya faru a tsakaninmu ɗazun. Jin ɗakin shiru kamar babu motsi ya sani ɗan ɗagowa ina kallon ko ina. Sauka idanuna sukai a kansa. Yana zaune a cikin sofa sanye da bathrobe alamar bai cire ba tunda ya fito wankan, bowl ne na glass a saman cinyarsa da uban chocolates a ciki. Da mamaki nake kallon chocolates ɗin kafin na ɗan ɗaga idanuna akan fuskarsa. Da farko na zata ma barci yake a hakan, sai da naga gashin idonsa dogaye sosai sun ɗan motsa alamar kallona yake ʙasa-ʙasa. Kauda nawa idanun nayi kamar zan juya naji ya furta, ā€œZo nanā€.
              Idanuna na ɗan rumtse, dan duk sanda saukar muryarsa zai shiga cikin kunnuwana sai na jisu har tsakkiyar brain ɗina. Sai da na ciza lips da sauke numfashi sannan na juya kaina a ʙasa na nufesa. Ban zauna a kujerar da yake ba doguwa sai na zauna akan ɗayar dake gefensa dan guda uku ne dama. Doguwa ɗaya sai biyu masu zaman ɗai ɗai a gefe da gefen ta.
         ā€œMi kike buʙata?ā€.
      Ya faɗa a daʙile yana kai sauran chocolate ɗin hannunsa ʙaramin bakinsa. Satar kallonsa nayi ina mamaki a raina, namiji da cin chocolate, ai kayan yara ne da mata, duk yau banga ni dai ya ci abinci ba, sai dai ko da suka fita yaci. Ganin ya zuba min ido na ɗan girgiza masa kaina da faɗin, ā€œBa komai, kawai na jika shiru ne baka fito ba. Ga kuma abinci duk yau naga baka ci baā€.
             Shiru bai tanka min ba tsahon kusan mintuna biyu, kafin ya ɗago a nutsensa zaune sosai tare da ajiye bowl ɗin chocolates ɗin nashi a Centre table. Murya can ʙasa ya ce, ā€œGashi ina ciā€. Yay maganar yana nuna bowl ɗin chocolates ɗin. Da mamaki na ɗago idanuna sosai na warosu a kansa. Tare da furta, ā€œChocolate ne abinci? Abin kwaɗayin yara ne fa. Kai kuma ʙatoto da kai ka zauna kana ci, kuma amma ce fa maza basa cin zaʙi hak…..ā€
           Ganin yanda yake kallona da mayatattun idanunsa na kasa ʙarasawa, sai ma na miʙe cikin wayancewa na ce, ā€œAn kira magrib bari na shirya kar su zo suna jiranaā€. Na wuce bayi da sauri.
         Da kallo ya bita harta shige, sai kuma ya girgiza kansa shima yana miʙewa zuwa closet ɗinsa yin shirin massalaci.
          
          šŸ’•šŸ’•šŸ’•

      Bayan sallar magrib Hayatu da kansa yazo ɗaukarmu. Ogan nasa bai dawo ba. Amma tunda shi yace zamuje dama sai ban damu ba na shirya tsaff cikin atamfa riga da skirt a kayan daya kawo min. Ni da Hafizzullah da Mama a baya, Yaya Musaddiq da Hayatu a gaba. Yanda naga bakinsa yaʙi rufuwa saboda farin ciki nasan Mama ta gaya masa komai ko mahaifinsa. Nayi matuʙar mamakin ganin ʙayataccen gidan da shima yake a ciki. Sai na sake yarda da batun Mama Balki da tace su suna zaune a Maash Mansion ne kawai saboda Ummie. Shine gaba muna biye da shi, sosai ta ciki ma gidan yay ʙyau da tsaruwa. Sai da muka zauna ya kwala kiran mai aikinsu wata Ę“ar budurwar yarinya ta fito. Gaishemu tayi sannan ya bata umarnin kawo ruwa da abinci shi kuma yay sama. Babu jimawa sai gashi ya fito riʙe da ʙyaʙyʙyawar matashiya, gaskiya zata iya girmata koda shekara uku ne, da ʙyar take tafiya saboda cikin jikinta da yay girma sosai. Duk da fuskarta ta ɗan yi fushi irin na masu ciki hakan bai ɓoye kammaninta da Hafizzullah ba. Yanda muka zuba mata ido haka itama ta zuba mana nata. Lokacin da suke isowa gab da mu jikinta har rawa yake yi. Haka ta dinga bimmu ɗaya bayan ɗaya da kallo, kafin ta maida kan Mama da ke kallonta itama fuskarta ɗauke da murmushi. Cikin langaɓar da kai ta ce, ā€œMama ina ji a jikina su ɗin jinina ne. Dan ALLAH Mama kada kuce dani ba haka bane ba. Yaya Hayat yace bazai faɗa ba sai dai na gani da ido naā€.
         Murmushi mukayi mu dukanmu, kafin Mama ta gyaɗa mata kai. ā€œTabbas su ɗin jininki ne Falaq. Ga babban yaya Musaddiq, sai Samraah ban ʙanwa, sai auta Hafizzullahā€.
         Kuka ta saki a hankali idonta akanmu muduka ta ce, ā€œWlhy yaya kamar Baba, suna kama sosaiā€. Ta faɗa tana sake fashewa da kuka mai ban tausayi. Gaba ɗaya muka miʙe muka rufu kanta. Yaya Musaddiq akwai son Ę“an uwansa, tuni ya janye ta daga jikin Hayatu ya kamata ya zaunar a kujera, gabanta ya durʙusa cikin lallashi yake mata daɗaɗan kalamai. Sai ta fara dariya ga hawaye. Ganin haka nima na zauna a kusa da ita na shiga share mata hawayen nata. Sai ta haɗamu ta rungume, tare da miʙawa Hafizzullah hannu alamar shima yazo. Ta ɗayan gefenta ya zauna shima muka haɗe kai waje guda muka bar Mama da Hayatu Ę“an kallo. Mun jima a haka kafin Mama su dinga lallashinmu. Sallar isha’i data gitta ya samu miʙewa, mazan suka fita mu kuma mukayi anan gida. Koda suka dawo sabon babin hira muka buɗe, Yaya Musaddiq da Mama nata bamu labarin Baba. Dan Hayatu fita yayi wai Maash ya kirashi akwai inda zasu je. Banyi mamaki ba, dan sukam ko aljanu haka suka gansu suka barsu saboda shegen yawonsu. Sai naji tausayin Falaq ya kamani, haka take haʙuri (kema haka zakiyi haʙurin) zuciyata ta ayyana min. Da mama ke sanarma Falaq ɗin ni matar Maash ce a yanzu wani irin ihun farin ciki ta saki tana rungumeni, koba komai Ę“ar uwarta ta dawo kusa da ita. Tsaff suka bata labarin yanda komai ya faru, ta dinga farin ciki da ʙorafin Hayatu ita bai sanar mata ba. Kamar wasa sai ga lokaci yaja. Dan sai da sha biyu tayi sannan Hayatu ya dawo, shine yake cewa ga Maash a waje yana jiranmu. Kuka Falaq ta sanya wai anan zamu kwana, ita bata gaji da ganinmu ba. Cikin dariya Hayatu yace, ā€œNikam babu ruwana Hubby, keda yayanki jeki gashi canā€.
         Aiko miʙewa tai tana ɗaukar mayafina, itako Mama Balki ta miʙe tana faɗin, ā€œA’a nidai kam nayi nanā€. Dariya muka sanya mata, dan muma ba son tafiyar muke ba, saboda hirar bata ishemu ba. Sai addu’a nake a zuciyata ALLAH yasa ya yarda. Kusan mintuna biyar sai gata ta dawo tana tuttura baki. Mayafina ta cire ta miʙamin tana faɗin, ā€œYa yarda da ʙyar su Yaya su kwana anan ɗin, amma wai ke kije lil sisā€¦ā€.
        ʁata fuska nayi nima kamar zanyi kuka. Nace, ā€œAmma baki roʙesa ba ko Aunty?ā€.
           ā€œALLAH har kuka na masa. Kin san taurin kan Yayana kuwa. Idan yace a babu mai canja masa zuwa b. Cayay da ma wai idan na haihu zaki zo. Bama gobefa kenanā€.
        Dariya Hafizzullah ya fashe da ita, harara na balla masa da ɗaukar mayafina fuuu na nufi hanyar fita…
         Shima dai Yaya Musaddiq da ke riʙe dariyarsa da Hayatu sai da suka dara, kafin su miʙe subi bayanta.
             Sanda suka iso ina tsaye jikin motar ta saitin inda yake ina masa magiya amma ɗan mannin bai ko buɗe idonsa dake lumshe ba ya kallan bare ya tanka. Haushi da takaici ya sani balla masa harara na koma ta ɗayan side ɗin dan Mama ce a gaba kusa da TJ, da sauri TJ ɗin dake a waje ya buɗen ʙofar yana wani risinawa. Ko kallonsa banyi ba na shiga na zauna na juya ʙeyata. Koda su Yaya Musaddiq suka iso wajen inaji yana magana da su wai ʙanwarsa ta masa fin ʙarfi shi da baʙi ita da ʙwacesu su kwana. Ina jin yanda suke Ę“ar dariya da bashi haʙuri. Basu wani jimaba yace ma TJ muje Mama ta gaji. Suna min sallama ʙin kallonsu nayi, ina jiyo dariyarsu su duka ukun sai naji idanuna sun cika da ʙwalla……..āœļø

    ALLAH ka gafartama iyayenmu šŸ˜­šŸ™

    *_TypingšŸ“²_*

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›

    (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    __š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†_ š‘·š’‚š’ˆš’† twenty five…

    …..Koda muka iso gidan na gama shiryama raina abinda zanyi. Dan haka ina fitowa na zabura zanyi sashen masu aiki caraf aka riʙeni. A fusace na juyo, sai dai kafin ma na samu damar cewa wani abu camak ya ɗagani a cikin hannunsa ko kunyar su Mama Balki da TJ da sauran ma’aikatan dake a harabar gidan da basu yi barci ba baiji ba. Salati na ɗauka ina wawwaro idanu na da suka cika da ʙwalla waje. Amma sai yay biris dani kamar ma baiji ba, takunsa ma yake ɗai-ɗai like bai ɗauki komai ba. Tafi mukaji da salati, da sauri na ɗaga ido na kalla saman ginin dan tanan ne ake yi. Sai ko idanun nawa suka sauka akan Hajiya Mammah dake tacan sama a balcony na upstairs. Mutsu-mutsun son sauka na farayi, amma ko alamar zai taimaka ya saukenin baiyi ba. Bai kuma nuna shi yama jita ba balle ya kalla inda take. Bai kuma direni ba sai a gaban ʙofar sashensa. Yana riʙe da hannuna ya buɗe muka shiga. Muna shiga falon na sakar masa kukan shagwaɓa ina faɗin, ā€œNi ka sakan min hannu wajen Ummie zani, kuma ka daina bani kunya gaban mutaneā€. Hanya ya nuna min alamar naje. Yanzu kam kasa haʙuri nayi sai da na kallesa. Sai kuma na shiga ʙyaʙyʙyafta idanu. Muryata na ɗan rawa na sake ɗagowa zanyi magana yay mun alamar zipping akan bakinsa tare da sake nuna min hanya. Kamar zan fasa kuka na shiga tafiya a hankali yana biye da ni har cikin bedroom. Koda muka shigan ma sake nuni yay min ba bathroom. Nan ma sum-sum na wuce dan babu alamar wasa a tattare da shi. Gaba ɗaya a tsorace nake, idan yace abinda ya aikata zai maimaita nama san mutuwa zanyi kawai.. Wankan nayi tare da ɗauro alwala amma sai na kasa fitowa duk da bathrobe na saka. Ina tsayen ina faman ʙullawa da kwancewa kawai ya shigo shikin bayin, idanu na waro sosai na mamaki, sai ya wani lumshe min idanunsa yana nufoni, da sauri naja da baya na manne da bango, na gama sadaʙarwa kaina zai zo sai kawai ya wuce ni. Ajiyar zuciya na sauke mai nauyi tare da fita a hanzarce cike da sassarfa. Na ji daɗin ganin kayan barci daya ajiye min wando da riga masu kauri, ɗauka nayi na saka a gurguje, tare da ɗaukar mayafina na yafa. Har na kammala abinda zanyi dan ya ɗan jima a cikin bayin sai kuma gashi ya fito sanye da bathrobe fara tas shima. Idanu muka haɗa, nai saurin ɗauke kaina ina sake ɓata fuska. Shima sai yay wucewarsa kamar bai ganni ba. Ya jima a cikin closet kafin ya fito nan ma, ina kwance kan sofa ina game da wayarsa daya ajiye a Centre table sai gashi ya fito shima cikin kayan barci sky blue da suka masa ʙyau sosai. Batare da ya kallan ba yace, ā€œMujeā€. Wani ɗan karan daɗi ne ya kamani, cike da zumuɗi na bisa dan a zatona ya barni naje can ɗin na kwana. Bare ma dana ganni a sashen Ummie ta hanyar da ban taɓa sanin yana da ita ba. Mun sami Ummie har tayi barci. Zama yay yana mata addu’a, ganin haka nima sai na zauna ina mata addu’ar. Tsahon mintuna goma sha muna a ɗakin ya fara riʙe kansa. Muʙewa yay a hankali tare da riʙo hannuna ya ce, ā€œLets goā€. Tsoro naji yanda naga ya riʙe kan, dan haka banyi musu ba na bisa. Sai da naga zamu koma sashensa nai ʙoʙarin yin magana amma ya hanani hakan. Muna shigowa a bakin gado ya kai zaune, yana sake dafe kan nasa da hannu bibbiyu. Tsoro ne ya kamani da tausayinsa, har bamma san naje gabansa na durʙusa ba ta tsakanin ʙafafunsa na dafa gwiwarsa ɗaya, ɗayan hannun kuma na kaisa saman nasa hannun daya dafe kai. A hankali na janye nasan muryata a raunane na ce, ā€œYa Awwab miya faru? Baka da lafiya ne?ā€. Shiru kamar bazai kulani ba, sai kuma ya ɗago shanyayun idanunsa da launinsu ya sauya zuwa golden yana kallona. Cikin motsa lips ɗinsa kamar baya so ya furta, ā€œMy headā€. ā€œCiwo yake?ā€.Idanunsa ya lunshe min alamar eh. Cikin damuwa nace, ā€œNa maka kamu?ā€. Nan ma kan kawai ya jinjina min yana maida idanunsa ya rufe. Miʙewa nayi sosai dan na fara gajiya da durʙuson, hannunsa na janye, na ɗaura nawa a wajen na fara masa addu’a. Inayi ina kamun da tofa masa addu’ar. Har na kammala ina faɗin, ā€œALLAH ya ʙara lafiyaā€. Ya amsa min da amin akan lips ɗinsa, ʙoʙarin barin gaban nasa nake naji saukar hannunsa a saman ʙuguna. Da sauri na kallesa tsigar jikina na tashi. ā€œIna zaki?ā€. A raunane na ce, ā€œSaman sofaā€.ā€œGadon fa?ā€.ā€œAmma….ā€. ā€œShiiiiii!!!ā€. Ya katseni tun kafin na ʙarasa faɗa. Tare da nuna min saman gadon babu wasa sam akan fuskarsa. Duk da shi dai ba banbance farin cikinsa ko damuwarsa kake dama a saman fuskar ba. Tunda akoda yaushe babu alamar fara’a a tare da shi. Sai idan shine ya so ya saki wannan munafukin murmushin nasa iya lips. Jikina har rawa yake wajen hawa gado. Idanuna kam tuni sun tara ʙwalla. Haka na kwanta ʙarshe gadon na wani naɗe jikina tamkar Ę“ar mage. Shiru banji ya hawo ba bai kuma tashi ba. Kaɗan na ɗan buɗe ido na kallesa. Yana zaunen har yanzu dafe da kan nasa alamar bai gama sauka ba. Jinai tausayinsa ya ʙara kamani, bamma san cikin raunin murya na furta, ā€œKo dai yunwa ce? Nifa duk yau banga kaci abinci baā€. Shiru baida alamar amsa min. Baima motsa a yanda yake ba har na gaji na maida idanuna na rufe. Mintuna baifi biyu ba ya hauro saman gadon, tuni zuciyata ya fara mutsu-mutsu, barema da ya kashe wutar ɗakin ya bar lamp ɗin side ɗinsa kawai itama ya maidata can ʙasa ba wani hasken kirki kasancewar muna a cikin net ne da yayma gadon rumfa gaba ɗaya. Jira kawai nake naji yamin irin na waccan ranar amma sai naji shiru baima ko matso inda nake ba. A hankali a hankali na fara samun nutsuwa har barci ya ɗan fara figata. Sai can na saki jikina sosai sannan na jisa a bayana. A ɗan firgice na farka, sai da ya riga har ya birkitoni na koma jikinsa gaba ɗayana ya rungumeni. Kasa daurewa nayi, sai da nayi magana cikin rawar murya irin ta wanda ke cikin tsoro. ā€œYaya wlhy akwai ciwoā€. ā€œNace zanyi wani abu neā€. Ya faɗa cikin kunnena da wata irin muryar da sai da tsigar jikina ta tashi. ʘam na runtse idanuna ban sake cewa komai ba. Shiru har kusan mintuna biyu muna a haka kafin a hankali ya dai-daita fuskata da tashi, goshinsa a saman nawa hakama hancinsa sai lips ɗinmu sai dai su ba’a haɗe ba. Duk da a cikin duhu-duhu muke yanda idanuna ke a rufe shima nasa a rufen suke. Cikin wani irin soft and low voice ya furta, ā€œYanzu dai so kike ayi wani abu ko?ā€. Da sauri na shiga girgiza masa kaina hawayen da nake riʙewa na zubowa da gudu. ā€œTo mi kike so?ā€. ā€œBarciā€.Na bashi amsa har ina taune lips ɗina jikina na tsuma. ā€œNi kuma bana jin barci ya za’ayi?ā€. A marairaice na ce, ā€œKa tashi kayi salla to ko karatun Alkur’aniā€. ā€œUhum-uhum. Ni matata nake buʙataā€. Har cikin tsakkiyar brain sai da naji saukar furucin. Muryata na matuʙar rawa na ce, ā€œYa Awwab wlhy akwai ciwo. Kuma doctor tace ba…bai…war…ke…b…..ā€ Nama kasa ʙarasawa. ā€œYanzu mi kike so ayi to?ā€. Da sauri na sake maimaita, ā€œBarciā€.ā€œKin tabbatar?ā€. Kaina na shiga jinjina masa. Da sauri-sauri. ā€œTom bari na saki barcinā€. Ya faɗa acan ʙasan maʙoshi. Kafinma nace wani abu naji saukar small lips ɗinsa kan nawa. Tun ina mutsu-mutsun ruɗewa da firgici har na nutsu luff, dan wani irin salo yake min mai shagaltar da gangar jiki, cikin ʙanʙanin lokaci na gama sallamawa gaba ɗaya na batare da ni kaina nama san minake ba. Ban tashi fahimtar kuskure na ba sai da aka ɗauki wani layi daban. Duk da a yanda yau yake bina a mugun nutse, cike da tattali da kulawa bamma san sanda na sakar masa kukan azaba ba jikina na matuʙar rawa…..

    ā¤ļøā˜…ā¤ļøā˜…ā¤ļø

    Tun a balcony ɗin take faman jera manya-manyan ashariya wa Maash. Koda ta afka bedroom ɗinta gaba ɗaya ta kasa haʙuri saboda yanda zuciyarta ke mata hanʙoro. Wai mi yaron nan ke shirin maidasu? Ƴan iska ko mi? Yanzu har Ummu-Hidaya ta haifi abinda zaifi ʙarfinsu kenan. Yarinyar da aka haifa a gabansu, balle shi karan kaɗa miya. Kai wlhy bazai yiwu ba. Dole ne ta ɓaro aikin da dolema ayita ta ʙare a gobe. Ina dalili Rubayya ta sakata aikata abinda ke neman juyewa da ita. Banda yaron nan ʙwallon ɗan iska ne ka haikema yarinya amma ka koma kana wani abubuwa irin ga matarka ɗin nan kayi first night ko. To wlhy daga daren yau zuwa gobe sai ta tada hankalin kowa na gidan nan sai dai anyita ta ʙare. Munafukai kowa yayi shiru da bakinsa irin komai ma bai faru ɗin nan ba. Waya ta jawo, ta shiga daddanawa. Number baba prof ta kira. Sai da ta kusa tsinkewa ya ɗauka cikin alamun wanda ya fara barci. Kuka ta fashe masa da shi a maimakon sallama. Cikin tashin hankali ya shiga tambayarta abinda ke faruwa?. Amma taʙi magana sai kuka. Sai da ya mata tsawa cikin tashin hankali kafin ta fara magana tana jan sheshsheka. ā€œBaba wace irin ʙazamar rayuwa kuma ke neman zuwa mana gidan nan. Mun shiga uku Awwab ya ɓalle. Baba kaga kuwa abinda na gani yanzun nan. Ya gama lalata wata gata can kwance a asibiti gashi can kuma yaja wata sashensa zai ʙara. Kuka yarinyar take tana roʙonsa amma bai barta ba. Har magana nayi masa amma ya hauni da zagi, wai bamun damesa yay aure ba, to haka zaita haye Ę“aĘ“an mutane har Ę“aĘ“anmu ma su jira zuwansa. Mu kammu idan bamu kama kammu a gidan nan ba sai layi ya biyo ta kanmu. Baba wlhy Awwab ya gama iskancewa, yaro ya tambaɗe ya lalace, kai ko jinin turawa na yawo a jikinsa. In baiyi bama ai bai cika jikan sifanawa ba (Spain šŸ˜‚). Wayyo Baba mun shiga ashirin watan zubewar mutuncinmu yazo a duniya. ʘilama a wannan karon har bbc saita bugamu…ā€ A rikice Baba yay mata tsawa, dan gaba ɗaya ta gama ruɗar da shi yama kasa yin tunanin daya dace. ʘitt ta yanke kiran tare da kashe wayar gaba ɗaya. Dariya ta sanya cikin yanayin basanci ta ce, ā€œA’a badai nice ba. Ai sai kaci baban uwarka Alonso Awwab. Gobe-gobe sai ka zama mijin Azizat ɗina. Kwantar da hankalinki Ę“ar albarka kukanki na kusa sharesa, nima kuma burina ya kusa cika.ā€ ta sake ʙyalʙyalewa da dariya…….āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›(Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    __š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†_š‘·š’‚š’ˆš’† twenty six

    ……Fita tayi a sashenta, kanta tsaye tai sashen Paah shima. Wani irin mahaukacin bugu ta dingama ʙofar tana kuka da ihun da sai da kusan kowa ya tashi. A masifar firgice Paah da Hajiya ʙarama suka fito. Ko bari su tambayi ma abinda ke faruwa batai ba ta hau rusar kuka da sanar musu kamar yanda ta sanar da Baba prof ta waya. Hankalin Paah da Hajiya ʙarama duk tashi yayi. Suka shiga salati da sallalami. Dai-dai nan sai ga kiran Baba prof ta wayar Uncle Abdullahi da suma bugun Hajiya Mammah ɗinne ya tashesu. Kururuwar da Hajiya Mammah keyi har yanzu ya sashi tsawatar musu kasancewar a hansfree Uncle Abdullahi ya saka wayar. ā€œMiyasa bazaku nutsu ba ne wai. Baku da hankali ne sai kowa ya fahimci abinda ke faruwa. Darene fa? Gida cike da ma’aikata. Idan abinda ke faruwa bai zama tonon sililin ba wannan shirmen naku da tatarako ai zai zama. Kowa ya wuce ya kwanta. In sha ALLAHU da safe zan shigo gidan zai ci ubansa ne aiā€. Kowa ya gamsu da bayaninsa, yayinda Hajiya Mammah ke kwasar dariya a zuciya. Paah kuwa jiri ma yake jin yana neman ɗibarsa. Sai da ya dafe bango dan tashin hankali. Ita kanta Hajiya ʘarama zuciyarta sai mutsu-mutsu take a ʙirji. Ji take kamar tayi tsuntsuwa a sashen masu aiki dan ta tabbatar ita dai ba Samraah ɗinta yaron nan ya sake haikemawa ba. Sai dai babu damar yin hakan. Dole ma sai itace ta kama Paah suka koma ciki. Uncle Abdullahi da matarsa ma suka koma nasu sashe. Itama Hajiya Mammah ta juya tana dariyar ʙeta. Ranta fes wlhy dan gwara ayita ta ʙare….. šŸ˜‚šŸ˜‚Hegiya Hajiya Mammah kin iya haɗa guri ko, to bari muga yaya wasan zai kaya🚓.

    šŸŒæā¤ļøšŸŒæā¤ļøšŸŒæ

    Ni a karan kaina ban san iya adadin kukan da naci ba. Dan gwara waccan ranar daga ʙarshe suma nayi, yau kuwa har ma fata nake ko zan suman na samu sassauci amma sumar taʙi zuwa. Azaba iya azaba da kwantata badai baki ba. Ban sani ba, ko hakan ya faru ne dalilin ina cikin tsoro da kuma ban gama farfaɗowa a waccan baʙar wahalarba oho. Duk da a yau komai yana yinsa gently ne ni banga wannan gentle ɗin ba sam. Kuka na gidan duniya na shashi har ina jin idanuna kansu sun min wani uban nauyi. Roʙo magiya harda cizonsa nayi amma bawan ALLAHn nan sai da ya kai inda yake buʙata. A Bathroom ma wani sabon kukan na sha, amma sam baiji tausayina ba sai da ya tabbatar ruwan zafin ya ratsani sosai yanda ya kamata sannan ya taimaka min na tsaftace jikina. Yanda ya ɗaukeni da kansa ya kai haka ya sake ɗakkoni ya maido saman gadon. Da ʙyar na amshi magani daya bani, ina gama sha ya kwantar dani, bamma san barcin wahala yay awan gaba dani ba. Dan tun ina jinsa sama-sama yana salla har nayi barcin ban san ya dawo saman gadon ya kwanta ba sai asuba…. ā˜…ā˜… Yanda Maash bai bari sunyi wani barcin kirki ba a wannan daren haka mafi yawan iyayensa basu runtsa ba. Hajiya Mammah dai na sake ʙulla abinda zata zo da shi gobe idan ALLAH ya kaimu. Paah na cikin tashin hankali da damuwa tare da nadamar abinda yake aikatawa. Dan shi kawai zuciyarsa na bashi TSUTSAR NAMA CE TA ZAMA NAMA. ʁarnar da yake aikatawa ce tai naso wa gudan jininsa. Shiyyasa masu iya magana ke cewa ƊAN GADO HAR YA ZARTA. A wannan gaɓar kam ya yarda. Dama ance zina na bibiyar jini, idan kayi da Ę“ar wani sai anyi da taka. To shi bashi da ɗiya mace, shine ALLAH ya jarabci ɗansa babba da wannan ta’asar da ʙila zata zama sanadin tashi fallasar shima. Harga ALLAH bai taɓa fyaɗe ma kowa ba, amma fa tun yana secondary school ya fara neman mata. Saboda irin rayuwar da suka tashi, rayuwar turai. Uwa babu kwaɓa uba ba tsanani. Dan Ummansu nada faɗa, amma gasu Ę“aĘ“anta soyayyace ziryan take musu. Garama mahaifinsu, yakan ɗan yi faɗan idan yaga abubuwan sunyi yawa. Shi kansa bai san adadin matan dayay mu’amala da su ba a rayuwarsa. Tun ma yanayin mai aji har gashi ya koma mu’amala da mai aiki. Dan da Siyama kawai yake mu’amala a gidan, hasalima ya santa ne tun kan ta fara aikin, koma yace saboda shi ta dawo aiki gidan, dan tace suyi aure yace a’a, shine ta zagaya ta samu aiki a gidan sai kawai ganinta yayi. Ya shiga matuʙar shock a lokacin, amma da yake Ę“ar duniya ce sai da ta maida shi ruwa a kanta duk da kuwa shi in har ya mu’amulanci mace ya rabu da ita da wahala ya koma. Amma akan Siyama sai tarihin ya canja, dan ta rantse masa in har yay sanadin data bar gidan sai ta tona masa asiri, shiyyasa ma ya barta saboda ya fahimci yarinyar hatsabibiya ce kwarai da gaske. Amma yau sai gashi ɗansa nayin yanda yaso a cikin gida batare da kunya ko shakkar wani ba. Ita ko Hajiya ʙarama tashin hankalinta kada ace Maash ya sake haikema Ę“ar gaban goshinta Samraah ne. Har bayi ta shiga ta gwada kiran Mama Balki sai kuma ta fasa, saboda tunawa da Mama Balki nada miji fa. Ita dai damuwarta kawai kada Maash ya sake taɓa mata yarinya. Acan Uncle Abdullahi da matarsa sun shiga wasi-wasi. Dan su zukatansu sun fara nusar da su anya kuwa ba magauta bane suka asirce Maash ɗin ke wannan irin ta’asar babu kunya babu tsoron ALLAH a cikin gida kamar wata rayuwar kafurci. Kai da sakal fa. Yaron nan na buʙatar manyan malaman ruʙuya a kansa. Ita dai Maman Malika ma harta fara batun maida Malika Niger sai abubuwa sun dai-daita. Idan har abinda Hajiya Mammah ta faɗa Awwab ɗin ya faɗa to lallai basuga ta zama ba kuwa. Dole abar gidan da Ę“ammatan yaran nan guda huɗu zankaɗa-zankaɗa. (šŸ˜‚Yayanmu kaga idi. Kowa zai fara killace ɗansa saboda kai🌚, wannan aiki yayi tsamari🤣). A ɓangaren Baba prof shima ba barcin daɗin ran yayi ba. Dan ya jima ma bai runtsa ba bayan ajiye wayar da yayi. Har gwada kiran wayar Maash yay amma ba’a ɗauka ba (šŸ˜‚ina zai ɗauka kuwa kandala ta kanainayesa, danginta na murna an kwace mana Yayanmu🄶). Haka ya dinga kai-kawo kamar mai Safa da marwa, sai da yaji ʙafafunsa na neman sagewa ya haʙura ya kwanta. Aiko asubar fari ya miʙe dan ko’a barcin nasa mafarkin Maash ɗin kawai yake yi ya haikema yarinyar mutane (kuji masifa🄱. Yo banda sa kai a uku kai tsoho ina ruwankašŸ˜).

    🩸🌟🩸🌟🩸

    Saukar iska mai sanyi akan idanuna ya sani buɗesu a hankali dan sun min nauyi jingim saboda kukan dana sha. Ga barci da nake ji matuʙa dan sam ɗan wanda nayi bai wadaceni ba. Dishi-dishi nake ganin abinda ke gab da ni, cigaba da huramin iskar ya sani ʙarasa buɗe idanun sosai. Fes suka shige cikin nasa da sukai wani irin fitowa blue sosai, hakama golden ɗin daya ratsasu ya sake yin garai-garai tamkar zinare na ʙyalli a cikin glass. A hankali na ʙoʙarin sake maida nawa zan kulle saboda wani irin kunya ne ya baibayeni. Cike da karsashi ya ɗaura soft hannunsa saman fuskata yana sake matso da tasa fuskar gab da tawa, har hancinmu na gogar juna. Da silent muryar nan tashi mai fita acan ʙasan maʙoshi kamar abin dole ya furta, ā€œNo! Baby. Open your eyesā€. Baki na taɓe kamar zanyi kuka. Cikin shagwaɓa da ban san ni kaina nayi ba na ce, ā€œI’m not babyā€. Sake manne fuskarsa da tawa yayi, tare da sake maida muryarsa can ʙasa ya ce, ā€œYes you are not ni shaida neā€. Yanda yay maganar yana kai hannunsa saman jikina da sauri na saka nawa na ɗan buge nasan ina sake ɓata fuska zan saki kukan. Na kuma janye fuskata da ga jikin tasa na juya baya. Zafin da naji ya sani sakin Ę“ar ʙaramar ʙara. A hankali ya kwanto ta bayana duk da ma ya rufeni gaba ɗaya Ę“ar tsitt dani a jikin nasa. A cikin kunnena ya furta, ā€œStill Pain?ā€. Maimakon amsa kuka na sakar masa. Sautin murmushinsa naji a cikin kunnena, sai kuma ya saka hannunsa a saman fuskar tawa ya shafo hawayen. Hannuna nasa na ture nashin in ʙara ʙarfin kukan. Baice komai ba ya miʙe, har nayi tunanin ya barni ne sai naga ya zagayo ta gabana. Duvet ɗin da nake ciki ya yaye, tare da duʙowa ya ɗagani gaba ɗaya. Luff na kwanta a jikinsa tare da lumshe idanuna. Sai da muka shiga bayin na buɗe ganin yana ʙoʙarin cewa zai min wankan ma. Da sauri cikin shagwaɓa na ce, ā€œNi ka fita zan iyaā€. ā€œKin tabbatar?ā€. Ya faɗa cikin tsatstsareni da idanu. Kaina kawai na jinjina masa. Shima sai baice komai ba ya juya ya fita, yana gab da ʙarasa ficewar ya ce, ā€œKi tabbatar kin shiga ruwan nanā€. Daga haka ya ficewarsa. Ajiyar zuciya na sauke mai ʙarfi, ni ba haushinsa nake ji ba. Tausayin kaina kawai nake ji, in dai haka zata cigaba da faruwa wlhy na kaɗe har ganye na. Dan al’amarin sam bashi da sauʙi. Ban cuci kaina ba na nutsu na gyara jikina yanda ya kamata, kamar kuma yanda Mama Balki ta koya min hakama Doctor. Sai kuma naji na ʙara jin nutsuwa. Wanka nayi na ɗauro alwala. Cikin sanɗa da jan ʙafa na fito. Naji daɗin ganin babu kowa a ɗakin, sai doguwar riga mara nauyi da hijjab dana samu a saman sofa. Ɗauka nayi cikin sauke ajiyar zuciya na saka dan har shida da wasu mintuna. Sallar asuba nayi, koda na idar duk yanda naso yin karatun Alqur’ani kasawa nai, anan inda nai sallar na ɓingire barci. Bamma san ya shigo ya ɗagani ya maida a saman gadon ba……….āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›_* _(Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†_ š‘·š’‚š’ˆš’†twenty- seven.

    …….Kamar yanda Baba prof yay alʙawari ʙarfe shida da kusan rabi a Maash Mansion ta masa. Sosai ma’aikatan gidan sukayi mamakin ganinsa da wannan uban safiya. A ʙasan rai kuma kowa na tunanin ko jikin Hajiya Babba ne ya sake motsawa. Dan in har ba ciwon Hajiya Babba ba baka ganin Baba prof ɗin a gidan sai dai wani babban dalili. Fitowarsa a mota dai-dai da fitowar Maash daga sashensa sanye cikin farare ɗin tas sports wear. Gefensa Laalah ne sai baʙin bluetooth daya manna a kunnesa ʙafarsa da sport shoes na kamfanin adidas. Kallon kallo aka tsaya tsakanin shi da Baba. Kafin shi Maash ɗin ya fara rissinar da nasa idon a yanayin nan nasa mai ban haushi. Inda Baban yake ya ʙarasa, ʙasa-ʙasa ya ce, ā€œGood morning grandpaā€. Danne komai Baba prof yayi, cike da kulawa ya amsa masa da, ā€œMorning dear, how was your night?ā€. A takaice ya ce masa, ā€œSo goodā€.ā€œHummm Masha ALLAH haka ake so ai. Amma inaga zaka bar fita Jogging ɗin nan kamar?ā€. Cikin wani irin tsare kakan nasa da ido ya furta, ā€œBut why?ā€. Haɗe fuska Baba prof yay dan karma ya masa gardama. Kai tsaye ya amsa masa da, ā€œNazo ne muyi magana mai muhimmanciā€. Shima fuska Maash ɗin ya ʙara tsukewa, tare da kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa baʙi mai ʙyau. Kansa ya ɗan girgiza fuskar na sake komawa tamau. ā€œNo grandpa am sorry. Ka shiga ciki, jus 30minutes am come backā€. Baima jira mi Baba prof ɗin zai ce ba ya raɓashi ya wuce. Matuʙar sosuwa ran Baba prof yayi, dan ko iya cewa komai baiyi ba ya bisa da kallo kawai shi da karen nasa. Sai guards ɗinsa da suka take masa baya. Gefen lips ɗinsa ya ɗan cija kawai yana nufar hanyar babban sashen. Duk ta inda ya gitta masu aiki zubewa suke suna gaishesa. Ɗaya bayan ɗaya masu gidan suka fara fitowa suna gaishesa suma tunda duk sun san da zuwansa. Su dai yaran basu san mike faruwa ba dan ko barci ba tashi sukai ba balle ai batun yin sallar asuba. Hajiya Mammah tayi zaram zata wuce kiran Maash Baba ya dakatar da ita. Sanar musu Maash ɗin ya fita yayi, amma yanzu zai dawo. Sai a lokacin Paah ya ɗan sauke ajiyar zuciya. Tashi yay ya haura sama ya duba Ummie. Barcinta ma take hankali kwance. Sai mama Balki dake ɗan siɗaɗowa da tayi sallar asuba ta gyara sashen ta mata wanka ta bata abinci. Cikin girmamawa ta gaida Baban. Shiko yanata faman saka mata albarka da wannan ʙoʙarin nata. Murmushi dai ta dinga yi ita dai kawai. Bayan ya dawo ʙasan suka ɗan fara tattaunawa akan al’amarin Maash ɗin. Hajiya Mammah nata sakko batun Azizat, acewarta hakan shine kawai maganin wannan matsala data kunno musu kai. Uncle Abdullahi ya bata goyon baya, shi dai Paah da farko shiru yayi, sai da Hajiya Mammah ta balbalesa da masifa ne ya ce shifa bawai baya so bane. Kawai yana tunanin ta yanda za’a sake tadawa Awwab ɗin maganar ne baya kuma anyita a watannin baya sai dai rai ya ɓaci kawai a banza. Kowa ya fahimci uzirin Paah ɗin, dan taurin kan Maash a bayyane yake ga kowa na gidan. Dan in fa har bashi yace zai yi abuba babu ubanda ya isa ya sanya shi ya yisa. Hajiya Mammah dai ta nuna musu wannan karon za’a masa zagir-zagir ne, dolene su nuna masa su suka haifesa ba shine ya haifesu ba. Domin kafa hujja aka aika Maman Malika wai taje sashen Maash ɗin ta duba wace yarinya ce ya kai. Taso noʙewa, amma girman suruki ya hanata dole ta miʙe ta tafi, babu jimawa ta dawo ta sanar musu yafa kulle ʙafarsa. ā€œTunda yasan miya ajiye ba dole ya kulle ʙofa ba. Ai mudai Ummu-Hidaya ta haifa mana bala’i cikin zuri’aā€. Duk da furucin Hajiya Mammah ɗin baima kowa daɗi a wajen ba babu wanda ya tanka mata. Kusan a dai-dai lokacin ne kuma Maash ɗin yake dawowa gidan. Yayi zufa sosai sai furzar da huci yake. Dan yayi amfani da ʙarancin lokacin ne yay gudu sosai. Kai tsaye ʙofar babban sashen ya nufa, bayan ya amshi bottle water ɗin sa da towel a hannun Shu’aibu, Laalah biye da shi ya shiga da sallama ciki-ciki. Tuni su Afrah dake gyaran sashen sun fara zubewa suna gaishesa da girmamawa. Sau ɗaya ya amsa musu kawai yana ʙarasawa ʙaramin falon da iyayen nasa suke, wanda in ba irin meeting ɗin nan ba da wahala ma kaga wani a cikinsa. Kasancewar an rabashi da glass ne da babban yasa ko damuwa da kai-kawon masu aikin basu yi ba. Dan ba’a jiyo magana, na waje kuma baya ganin na ciki, na ciki ne ke hango ma waje. Kowa bai kalla a cikinsu ba ya kai zaune a kujerar farkon shiga falon da babu kowa a kai. Ruwansa ya ɗaga sama yana tsiyayawa a baki kamar daya shigo bai ga kowa ba. Sai da ya sha sosai ya ajiye a gabansa, karensa nata gefen ʙafafunsa ya kwanta shima yana huttan gudun da suka sha yau ɗin. Sai lokacin ya ɗan kalla iyayen nasa da duk suka zuba masa ido. A taʙaice ya janye yana cigaba da goge wuyansa zuwa ʙeyarsa ya furta, ā€œGood Morningā€ Paah ɗin ne kawai ya iya ʙarfin halin amsa masa da Uncle Abdullahi da Maman Malika. Amma Hajiya ʙarama da Hajiya Mammah wani shegen kallo suke binsa da shi. Na Hajiya ʙarama ba’a bayyane ba, amma ita Hajiya Mammah kamar idanunta zasu faɗo kansa. A masife ta ce, ā€œEh ai ba sai ka nuna mana kai tarbiyanka bai cikaba Awwab. Mune kakema gaisuwa like wasu sa’anninka ko. Kaje ai duniya ce zaka gani, wanda baima zo ba jiransa takeā€. Ko kallon inda take baiyi ba ma. Sai zamansa ya gyara cike da ʙasaita yay crossing ʙafafunsa ya jingina kansa da kujera ya wani lumshe idanu. Takaici, baʙin ciki, haushi. Babu wanda bai kumesu ba. Sai dai babu wanda ya tanka sai Baba prof ne ya ce, ā€œAwwab!ā€. Batare da ya ɗago ba ko gyara zamansa ya ce, ā€œNa’amā€. Sake danne zuciya Baba prof yayi ya cigaba da faɗin, magana ce mai muhimmanci ta taramu anan, kuma amsa muke buʙata daga bakinka, ba wannan shirun naka ba. Wancan karon kata mana zame-zame, na barka ne kawai dan na tabbatar da abinda akace kayin, ashe kuwa bazaka fasa ba tunda gashi ka maimaita. Kana ganin wannan rayuwar ta dace da kai kuwa Awwab, kaifa muka dinga fama da kai yin aure watannin baya amma ka nuna baka buʙata, why kuma yanzu ka zaɓi wannan rayuwar? Bayan tako ina ALLAH bai tauyeka ga yin auren ba? Na farko ya faru, anyi na biyu, to baza’a sake na uku ba, dan haka mun yanke shawarar daga nan zuwa next month za’a ɗaura maka aure da Ę“ar uwarka tunda a wata kusan tara ka kasa samo matar sai ka fara shiriā€. Wani shegen murmushi Maash ya saki a bazata. Dukansu sai da murmushin ya basu mamaki, hakan yasa duk suka zuba masa ido cikin ɓacin rai. Kasa haʙuri baba prof yayi yanzu kam cikin ɓacin rai ya furta, ā€œOh dariya ma na baka ko?ā€. Murmushin ya sake saki yana mai buɗe manyan idanunsa a kansu. Yanda sukai wani tar-tar blue ɗin ya fito sosai zai tabbatar maka da baya tare da kowace irin damuwa. Cikin halin ko’in kula ya ɗan lumshe idanun ya buɗe, tare da motsa lips ɗinsa a nutsensa ya furta, ā€œShike nan zan iya tafiya?ā€. Yanzun kam hatta Paah sai da ya zuba masa ido. Yayinda cikin masifa Hajiya Mammah ta shiga tafa hannaye da jera salati. Ta ce, ā€œNi Nafisa ALLAH kana gani, Awwab wai anya kuwa kai kam ba shaiɗani bane? Gaba ɗaya neman maida mu watsatstsu kakeyi ma dai na kula. Yanzu nan a duk zantukan nan da baba yay maka saboda sheɗanci da raini baka da abin cewa. Magana ta ALLAH Mu’azz ka haifa mana jaraba a familyā€. Ko motsi baiyi ba balle yama nuna yasan mi take cewa, sai da yaja fin mintuna biyu sannan ya wani irin buɗe idanunsa, kai tsaye a kanta ya sauke su, cikin wani irin salon kallon raini, gaba ɗaya sai ta daburce ta fara kame-kame da zaginsa. Ɗauke kansa yay daga gareta ya maida kan Baba prof, cikin motsa lips a daʙile ya furta, ā€œDaga farkon fara wasan har zuwa yau ai duk itace Director, ni ina amsa sunan actor ne kawai. Dukan amsoshin da kuke son ji a gareni ita ke da su.ā€ Wani irin kuka Hajiya Mammah ta fashe da shi tana zagin Maash da yaɓo maganar da duk tazo bakinta. Ko kallo bata sake isarshi ba ya miʙe abinsa yana mai ɗaukar bottle water ɗin sa. Da sauri Laalah ya miʙe shima. Cike da takun nan nasa na ʙasaita ya nufi ʙofa sai da ya kama ʙofa zai buɗe sai kuma ya ɗan dakata, kamar wanda yay mantuwa ya juyo, ā€œOh nace ba. Zan baki first and last warning. Idan kikace zaki cigaba da bin sawuna, wlhy wataran sai taɓo mai danʙo ya riʙe miki ʙafa ta yanda har sai naje na dawo daga inda zanje na sake dilmiyaki a ciki, kona datse ʙafafun kowa ya huta.ā€ ya kare maganar cikin karkaɗa yatsarsa, daga haka yay ficewarsa kamar baiga kallon da suke binsa da shi ba………āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›_*

    (Itama nama ce)__

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’† _š‘·š’‚š’ˆš’† twenty-eight

    …….Tsuru-tsuru kawai sukayi suna bin ʙofar da kallo, sai Hajiya Mammah ce ke zazzaga masifa cikin borin kunya. Dan sosai maganarsa ta ʙarshe ta wani irin shigarta. Ganin kallon da Baba prof ke mata yasa ta miʙe. Murya a ɗan zafafe ya ce, ā€œKoma ki zauna Nafisaā€. ā€œAmma Baba kana fa jin abinda ya faɗa min, wlhy sai naci uwar yaron nan a gidan nan. Yanzu har lalacewar wannan gidan takai kamar Awwab ya gaya min baʙaʙen magana a gaban Mu’azz amma yay kamar baima ji ba. Ba shi ba hatta uwarsa a gabana aka haifeta.ā€ Cikin damuwa da ɗan ɓacin rai Paah ya ce, ā€œAmma Adda mi kike so nace muku?. Duk dai mai hankali yaji wannan furucin na Muhammad zai fahimci akwai wani abu a tsakaninku ke da shi. Tabbas Muhammad bashi da ragowa, kuma in ransa ya ɓaci komai yazo bakinsa faɗa yake, amma tunda muke da shi bai taɓa maidama wani murtani ba a cikinmu sai yau. Duk kuwa abinda kiga Muhammad ya magantu a kansa to lallai wannan abun ya kai karen kure. Kuma ni kam gaskiya zuwa yanzu zuciyata ta fara bani akwai abinda yaron nan ke ɓoye mana, inda ace abinda ya faru a farko ne kawai zan iya yarda ʙaddara ta kaisa ga aikatawa. Amma muyi tunani, Muhammad fa duk da tsagerancinsa bazai zauna yana lalata yara ba irin haka a cikin gidan nan, dan duk da mahaifiyarsa na’a halin rashin lafiya bai haɗa mutuntakarta da komai ba. Mudai ʙara bincike gaskiya. Domin mu dukanmu mun san waye Muhammadā€. Da ga haka ya miʙe abinsa ya fice shima. Shiru falon yay babu wanda ya iya motsawa. Sai Hajiya Mammah dake wani irin cika da batsewa da famar jinjina kai. Ta bakin baba prof kowa ke son ji amma babu alamar zai ce wani abu. Sai ma miʙewa da yay shima ya fice a binsa. Ganin haka shima Uncle Abdullahi da Matarsa suka miʙe. Wani irin shegen murmushi Hajiya ʘarama da ke kallon Hajiya Mammah ta ʙasan ido ta saki, sai kuma ta mike itama batare da tace komai ba ta fita. Dan ta ciki na ciki ne kawai…..

    🪓🪓🪓🪓

    Watanni huɗu kenan Mamy na gida, babu labarin Mansoor tako ina. Gashi Dad baizo gida ba kuma kowa bai sanar mata ya saketa ba ko bai saketa ba. Gaba ɗaya ta fige ta rame saboda damuwa. Dan har ga ALLAH tana matuʙar so da ʙaunar mijinta. Ta tura masa text message yafi sau dubu. Ta kirashi yafi sau dubu goma. Amma babu amsa babu reply na masseges ɗinta. Ga ciwo ya addabeta a tsaitsaye har dai sai da ta kaita da kwana asibiti ranar. ALLAH sarki Attahiru shine tsaye akan komai. Ganin fa yanda jikin Mamy yay tsamari a wannan karon yaje ga Dad ɗin su ya dinga kuka yana roʙonsa ya yafe mata, sannan ko sau ɗaya yazo ya ganta. Dan sam Mamy bata a cikin hayyacinta. Babu abinda take faɗi sai neman gafarar Dad ɗin. Da farko Dad koran Attahiru yayi, sai da yaga yanda ya riʙe ʙafafun nasa yana rabzar kukan abin tausayi sannan. Dan har ga ALLAH a yanzu tausayin babban ɗan nashi yake yi. Attahir akwai haʙuri, gashi da son Ę“an uwansa. Ga biyayya a gare su. Yanzu tunda aka fara abin nan yazo neman ma Mamy afuwa ya masa gargaɗin kada ya sake masa maganar ta bai sake koda kwatantawa ba duk da abin na damunsa. Amma kullum dare yana lura da shi sai yaci kuka. Haka kuma zaita salla yana neman ɗaukin UBANGIJI da yima Mansoor addu’ar ALLAH ya karesa a duk inda yake. Shima sai hakan yaja hankalinsa yake tashi yin ibadar daren. Yanzu da yake roʙonsa duk sai jikinsa yay sanyi, kamashi yay ya rungume. Sun jima a haka kafin ta ɗagosa yana lallashi. Ya kuma tasashi gaba suka je asibiti suka duba Mamy. Abinda Dad ɗin yayi ya faranta ran kowa. Dan duk wanda yasan Mamy yasan ta horu da horonsa matuʙa. Wannan zuwa na Dad shi ya kawo masalaha ga ciwon Mamy, ta dinga jin sauʙi har al’amura suka fara daidaita. Koda aka sallameta sai suka koma gida. Nan ma ta cigaba da roʙon Dad ɗin gafara yaran suka tayata har sai da yace mata ya yafe mata. Ya kuma kafa mata sharuɗa da dokoki. Ko guda ɗaya kuwa bata musa ba a ciki. Doka ta farko data fara bi shine shiryawa sukaje har gidan Abba suka bashi haʙuri tare da neman gafarar Abban da sauran mutanen Gwarzo da basu wuce ba da su Gwaggo Gudidi. Sun so ganin Yaya Musaddiq aka sanar musu ai ya wuce Chaina yau ne ma ranar tafiyar tasa zai bi ta Lagos. Abin ya basu mamaki. Sun kuma tayashi murna. Sun kuma yi alkawarin zuwa weekend zasu je har gwarzo domin bama su Kawu Musa haʙuri, dan su tunda suka zo aka ɗaura aure da su suka kama gabansu tunda bikin bana ɓangaren su bane ba. Wannan ban haʙuri da su Mamy suka zo sukayi har gida ga ʙonama Mom rai, dama ga baʙin cikin tafiyar Yaya Musaddiq na cimata zuciya. Har ta kasa haɗiyewa sai da tai ta zabga habaici. Da yake dama Abba a ʙufule yake da ita akan tafiyar Baby basu bari ta masa sallama tama danginsa ba ya ce idan har Mom ta sake cewa ko uff a bakin aurenta. Dan ya tsinke sauran igiyoyin biyu da suka rage. Wannan magana ta matuʙar girgiza Mom da duk danginta. Nan fa suka shiga tausarta da nuna mata kuskurenta. Daga nan akayi zaman sasanci aka sakata bama Abban haʙuri da su Gwaggo Gudidi….

    šŸŒœšŸŒœā¤ļøšŸŒ›šŸŒ› ki

    Tunda ya shigo ɗakin yay tsaye kawai yana kallonta nannaɗe a ʙasa kamar Ę“ar mage. Barcinta take hankali kwance. Kaɗan ya ɗan jaa idanunsa kamar zai lumshe sai kuma ya buɗe. Durʙusowa yay ya ɗauketa gaba ɗayanta ya maida a saman gado, kafin ya shiga ʙoʙarin zame mata hijjab ɗin. Firgigit ta buɗe idanunta dake jajur duk sun ɗan kumburo alamar anci kuka an gode ALLAH. Sosai ʙirjina ya shiga bugawa da sauri-sauri ganin yanda ya ranʙwafo kaina, zaram nayi ʙoʙarin tashi jikina na rawa, sai dai zafin daya ratsani ya sani komawa da sauri na kwanta hawaye na ziraro min. Cikin ɗan jujjuya masa kai, lips ɗina da suka sha wahala a wajensa na rawa muryata a ɗashe na ce, ā€œPlease Ya Awwab don’t do wahala for me again. Wlhy zan iya mutuwa. I’m just 23years only zakai child abuse faā€. Shiru bashi da alamar cewa uffan, sai idanunsa masu tsananin kaifi da ya zuba min kawai kamar zai cinyeni da su. Cikin kuka sosai na sake buɗe baki zanyi magana ya ɗaura yatsarsa manuniya akan lips ɗin nawa yana mai sake matso da fuskarsa gab da tawa ya ce, ā€œShiii! Oya sleepā€. Ya ʙare maganar can cikin maʙoshi da ɗaura hannunsa ya rufe idanuna. Babu musu na rufe ɗin duk da a cikin tsoro nake. Tun ina ɗari-ɗari har wani barci mai daɗin tsiya yay awan gaba da ni saboda yanda yake shafa kaina a hankali. Ganin yanda ta fara sauke numfashi a hankali alamar tayi barci ya sashi yin ɗan guntun murmushi. A hankali ya furta, ā€œYou are a tiger, Samrhā€. Sai kuma ya sake sakin murmushin gefen baki saboda tuno kalmar child abuse data faɗa. Sam yarinyar nan bata jin magana. Ga baki kaman parrot. Vibration ɗin da wayarsa keyi alamar shigowar kira ya katsesa da ga kallon da yake mata. Dan kallon wayar yay dake a kan side drawer. Sai da ta kusan tsinkewa kamar abin dole kafin ya kai hannu ya ɗauka. Ɗagawa yay ya kai kunnensa yana ʙoʙarin barin wajen. Koda Juliet da tai kiran ta gaishesa a taʙaice ya amsa mata. Bata damu ba ta fara masa bayani kan aikin da ya sakata. Ta tabbatar masa ta kammala komai yanzu haka jirgin da zai taho da shi ya ɗakko hanyar Nigeria. Cikin wani irin yanayi mai wahalar fassara ya lumshe idanunsa dake canja launi. Shi kaɗai ya san mi yake ji a zuciyarsa, amma zai jure in sha ALLAHU. Sunayin sallama kiran Hayatu na shigowa. Gaisawa sukai shima sannan ya bama su Yaya Musaddiq suka gaisa. Kasancewar tafiyar ta Musaddiq sai dare ma ya bama Hayatun umarnin zagayawa da su suga gari zuwa anjima sai ya kawosu nan. Dan yau shi bazai fita ko ina ba zai yini a gida. Murmushi Hayatu yayi da ga can, amma duk da haka sai da ya tambayesa ko baida lafiya. Dan yasan abinda zai iya hana ogansa kuma yayansa fita ba ʙarami bane. A taʙaice yace masa no kawai ya yanke wayar, Hayatu ya jima shiru yana nazari sai kuma yay Ę“ar dariya. Anya kuwa! Anya ogan nasa bai faɗa lobayyar pepper ʙanwar tasu ɗin nan ba. Rashin mai bashi amsa ya sashi haɗiye komai ya cigaba da sabgarsa. Shi kam koda ya kammala wayar shiru yay a cikin kujerar lafe na kusan mintuna ashirin, kafin ya miʙe a hankali ya bi ʙofar dake sadashi da Ummie, ko’ina fes sai ʙamshi yake, ganin kwanikan abinci ya sashi tabbatar da har ta karya. Kusa da ita ya ɗan zauna ya shafa kanta dan barcinta take hankali kwance. Ga wani irin annuri da fuskanta keyi ʙyawunta da dauɗa ya dusashe na sake fitowa. Hawaye ne ya cika masa idanu, amma sai ya haɗiye su dan Ę“an mazan maza ne akoda yaushe. Ya ɗan jima a ɗakin har Mama Balki tazo ta samesa duk da yanda kansa ke juya masa da ciwo. Bayan sun gaisa yana ʙoʙarin danne damuwarsa da ciwon da kansa ke masa yay mata bayanin a saka cikin yaran can wasu su gyara sashen Fahad. Yana gama faɗa ya miʙe da sauri ya fice a ɗakin kamar wanda ake tunzurawa. Da kallo Mama da har tsigar jikinta ke tashi da jin wannan batu ta bisa. Sai hawaye sharrr suka shiga ɓulɓulo mata, ga murmushin farin ciki. Wani irin ʙaunar Samraah na ratsa mata zuciya. Yarinyar nan ta cika alʙawarinta kenan. Dan dama ta mata alʙawarin sai ta masa maganar dawowar Fahad ɗin gida. Kasa haʙuri tayi sai da ta koma ta sanarma mijinta. Shima farin cikin ne ya dabaibayesa har murmushi ya gagara barin fuskarsa. Ranar da wannan farin cikin suka yini, tuni kuma an saka masu aiki gyaran sashen Fahad dake manne dana Maash ɗin batare da kowa ya sani a gidan ba. Dan su suna can ma ran kowa ɓace da abinda Maash ɗin ya musu yau……..āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›_* _(Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†

    _š‘·š’‚š’ˆš’† twenty-nine…

    ..A hankali Maman Malika da tun da suka dawo sashensu ta ɗago ta kalla mijinta. Shima dai zaune yake shiru da alama akwai abinda yake tunani. Agogo ta kalla sannan ta sake kallonsa. Murya a sanyaye ta ce, ā€œAbban Muhseen yau bazaka fita aiki bane wai? Time fa yaja sosaiā€. Numfashi ya sauke a hankali, kafin ya kalleta fuskarsa na nuna damuwa sosai. ā€œZanje Mubeena. Al’amarin gidan nan ne ya fara damuna wlhy. Daga wannan sai wannan. Ga yaron nan sam baya ganin girmanmu. Shi kuma Yaya baya ʙaunar laifinsa sai ma kiga kamar yana tsoron sa.ā€ ā€œHumm Abban Muhseen ba tsoro bane ba. Sannan wlhy Awwab bawai baida mutunci bane ko kunya. Yaron yana cikin damuwa matuʙa. Ku kuma kun kasa fahimtar hakan. Kowannenku abinda ke gabansa kawai yake yi. Yanzu ko maganar nan daya gayama Adda fa abin a dubace. Dan babu rami miya kawo rami? Tabbas akwai abinda Addar ta sani game da abinda ke faruwa. Idan fa baka manta ba ko waccan ranar ita ta fara fasa zancen yama yarinya fyaɗe, duk da ana cikin tashin hankalin zuwa kamashi ita ba wannan bane damuwarta. Yau kuma itace fa ta tashemu a barci jiya. ʘarfe sha biyu da wani abu bata kwanta ba mi take yi? A barshi ma batai barcin ba, miya kaita sashen Awwab har tasan yana aikata wani abu? Mufa buɗe zukatanmu mu kalla gaskiya a matsayin gaskiya in ba hakaba ALLAH zamu yi dana sani. Kadai san halin Adda ai da fitinarta, musamman daya kasance burinta a gidan nan Awwab ya auri Azizat. Baka tunanin zata iya shirya komai dan hakan ta kasance tunda an bisa ta lalama, an bisa ta tsiya duk yaʙi. Sannan na fara ji a jikina akwai abinda Awwab ke ɓoyewa a gidan nan. Babu yanda za’ai duk rashin kunyarsa ya dinga lalata yara a cikin gida mudai nemo gaskiya.ā€ Sosai maganganunta suka shigi Uncle Abdullahi. Yay shiru yana nazarin kowane harafi dalla-dalla da yi masa fashin baʙi….

    🪓🌼🪓🌼🪓

    Tunda ta iso asibitin ta gagara taɓuka komai. Sosai abinda ya faru a gidan keta mata faman kai kawo a zuciya. Kalaman Awwab sun farkar da ita wasu abubuwa. Tabbas sau biyu tana kama Hajiya Mammah ta fito a sashen Awwab, na farko ranar da ta aiki Yarinyar nan da abinci, na biyu daren ranar da abin ya faru kusan misalin ʙarfe ɗaya ta fito daga ta backyard kamar wacce ke a firgice. Abinda yasa a lokacin bata maida hankalinta a kanta ba itama daga wani waje ta dawo. Abu na uku Hajiya Mammah ta damu akan zancen fyaɗen nan a safiyar ranar, sannan jiya ma itace tazo musu da zancen ga Awwab da wata. Da farko bata damu ba, sai yau da safe data bincika yarinyar nan a sashen masu aiki akace mata bata dawo ba ai. Bata samu damar ʙarasa binciken ba Baba prof ya iso gidan.. Mikewa tai tana mai girgiza kanta, dolene taje ta ʙarasa binciken data fara kafin wankin hula ya kaita dare. Daga nan tana buʙatar yin magana da Yallaɓai a wannan gaɓar. Handbag ɗinta ta ɗauka ta fice a office ɗin. Ko kallon tulin patients ɗin dake zaman jiranta batai ba dan hankalinta ma baya a kansu gaba ɗaya…..

    āœØšŸ’žāœØšŸ’žāœØ

    Barci sosai nasha. Dan ban tashi farkawa ba sai wajen sha biyu. A hankali na buɗe idanuna bakina na ambaton sunan ALLAH da karanto addu’ar tashi a barci kafin na yunʙura da ʙyar na tashi zaune saboda ciwon da illahirin jikina ke mun. Sam banyi tunanin yana a ɗakin ba, dan haka na miʙe cikin ʙarfin hali saboda wani irin fitsari nake ji sosai. Wani irin motsawa zuciyata tayi sakamakon saukar idanuna a kansa. Zaune yake cikin sofa kamar wani saraki. Laptop ɗin jarabar a saman ʙafarsa sai dai ya saka throw pillow sannan ya ɗaurata. Ta gefensa a saman side table ɗin kujerar bowl ne da chocolate a ciki sai mug alamar ansha coffee ko tea. Ledojin chocolate ɗin da yaci ya zubar a ʙasan na bi da kallo, haka kawai sai naji tausayinsa ya kamani. Dan abinda na fara fahimta da shi kamar bai damu da cin abinci ba sai waɗan nan tarkacen kayan chocolate ɗin. Tabbas koda ace bai son cin abincin akwai ʙarancin gatan mai tsayawa ya bashi ya ɗin.. ganin ya ɗan dakata da danna keyboard ɗin computer ɗin alamar yaji a jikinsa ana kallonsa ya sani saurin kauda idanuna da ʙoʙarin son barin wajen, a ko dai-dai nan ya ɗago manyan idanunsa ya sauke a kaina. Basarwa nayi kamar ban gansa ba na wuce bathroom ɗin. Ina shiga na jingina da ʙofa ina mai sauke ajiyar zuciya mai nauyi da godema ALLAH da ya taimaken bai kamani ina kallonsa ba. Wanka nayi da ruwa mai ɗumi sosai na sake gyara jikina yanda ya kamata, dan har ruwan zafin na shiga. Yau banyin walha ba ina barci, alwala nayi dan naga har sha biyu da kusan rabi yanzu. Hankalina duk yana akan su Yaya Musaddiq shiyyasa ban zauna wani noʙe-noʙe ba na fito sanye cikin bathrobe ɗin sa sky blue. Inda na barsa anan na samesa. Sai da na zo gab da shi ya ɗago kai ya kallan. Murya a sanyaye alamar nasha kuka batare dana kallesa ba na ce, ā€œIna yiniā€. Bai amsa min ba, sai idanunsa masu azabar kaifi daya zuba min. Ji nai duk ina neman daburcewa, dan haka nai ʙoʙarin barin wajen amma sai ya miʙa min hannu alamar nazo. Jinai kawai bazan iya musa masa ba, a hankali na fara takawa zuwa garesa, ɗan nesa kadan da shi na tsaya kaina a ʙasa. Soft hannunsa ya ɗaura akan nawa da nake wasa da su ya matsoni gabansa sosai, a bazata na jini zaune a saman cinyarsa alamar ya ajiye laptop ɗin da pillow ɗin. Sake matsoni yay cikin jikin nasa ya rungume tsam har ina iya jin bugun zuciyarsa kaɗan-kaɗan. Luff nayi wata nutsuwa na ratsani. ā€œYaya jikin ya daina zafi?ā€. Ya faɗa cikin silent muryansa a cikin kunnena. Sosai kunya ya sake ʙamani, maimakon amsa masa sai na sake ʙanʙamesa ina ɓoye fuskana a jikin nasa. Kaɗan naji yunʙurin murmushin sa cikin ʙirjinsa. Shiru kusan mintuna biyu ya sake furta, ā€œKona duba ne?ā€. Kafaɗa na maʙe masa da faɗin, ā€œUhm-uhmā€ cikin shagwaɓa ina ʙoʙarin tashi. Amma sai ya hanani yin hakan, hannayena ya kama cikin nashi ya zubama fuskata ido sosai yana kallo. Kasa kallonsa nayi ni dan bazan iya jurewa ba sam. A hakan ma ji nake kamar na gudu. Sake maida muryarsa ʙasan maʙoshi yay da kai hannu a haɓata ya ɗago fuskata da ʙyau ya ce, ā€œLook at meā€. Da ʙyar na iya ɗago idanun na kallesan. Cikin ɗan ɗage gira ya ce, ā€œShin bakin Ę“ar mutan Gwarzo ya mutu ne kwana biyu?ā€. Bakin na ɗan tura masa kaɗan. Girarsa ya ɗan ʙara ɗagewa da jinjina kai ya ce, ā€œI see, bai mutu ba ashe. Yanzu idan su Ya Musaddiq suka zo mi zaki ce da su ya samu wannan idanun da ya kumbura?ā€. Karan farko na ɗago na kallesa. Idanun nawa ya sarʙe cikin nashi, kallon juna muke cikin wani yanayi mai wahalar fassara. Jin yanda tsigar jikina ke tashi jinina na yamutsawa ya sani lumshe nawa a hankali. Murya ʙasa-ʙasa kamar mai koyan magana na ce, ā€œZan ce kai neā€. Na ʙare maganar in ɗan buɗe idanuna kaɗan. ā€œWhat a surprise, ni ne fa? To nayi me?ā€. Ai babu shiri na buɗe idanun gaba ɗaya ina harararsa da tura baki. Sai kuma na yunʙura zan tashi ina ʙunʙuni. Sake maidani yay ya zaunar ya ce. ā€œAnswer meā€.Shagwaɓe fuska nayi ina kaucema kallonsa na ce, ā€œNi dai ba ruwana. Ka sakan na saka kaya na je na ga Ummie naā€. Ɗan lumshe idanunsa yay ya sake buɗewa, sai kuma ya ɗan sauke numfashi, kamar wanda ke shirin sakin murmushi ya ɗan taɓe baki. Yatsun hamnuna dake cikin nasa ya ɗan matsa da murza farcen. ā€œShi wannan hannun yaushe za’a masa lalle?ā€. Hannun na kalla nima, sai kuma a hankali nace, ā€œAi babu lalli ne. Da dai nasan su Yaya zasu zo da sunzo min da shi. Kuma ma ina son wanke kaina ya fara cushewa.ā€ Kansa ya jinjina min alamar amsawar kenan. Nima sai nai ʙoʙarin miʙewa. Taimaka min yay na tashi, ina shirin barin wajen shi kuma zai maida laptop ɗin sa a ʙafa ya ce, ā€œMi zaki ci?ā€. Kallonsa na ɗan juyo nayi muka haɗa ido, sai kuma na kalla ledodin chocolates ɗin da yasha batare da nayi magana ba na nuna su. Idanunsa ya ɗan ʙanʙance a kaina. Sai kuma ya girgiza min kai a daʙilen nan nasa. ā€œKince ba abinci bane aiā€. ā€œTo kaima ai shi kake ciā€. ā€œHummā€.Kawai yace ya maida kansa ga wayarsa daya ɗauka. Ganin ya kai kunne alamar wani ya kira ya sa na wuce abina dan na shirya. Ban wani jima ba na fito cikin skirt da riga na atamfa. Sosai kayan sun min ʙyau tare da fiddo ainahin surar jikina. Ni kaina sai da na sakarma kaina murmushi ta cikin mirror. Dauri nayi mai sauʙi bayan na shafa turarensa da mansa. Koda na juyo sai na samu ni yake kallo shima. Da sauri na ɗauke kaina kunya na kamani. A ɗan daburce nace, ā€œZanje can sashen na ɗakko kayan kwalliyana Please Ya Awwab.ā€ Sai da ya maida kansa ga aikinsa kamar bazai kulani ba kafin a hankali ya ce, ā€œNoā€. Baki na ɗan tura batare dana sake cewa komai ba na nufi gadon. Tsaff na gyarashi, na tattare net ɗin. Dai-dai nan shima ya miʙe ya shiga bathroom. Babu jimawa ya fito alamar yin alwala………āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›_* _(Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    __š‘©š’š’š’Œ 3 _š‘·š’‚š’ˆš’†- thirty.

    .

    ….Ina a inda ya tashi ina gyara wajen da tattare ledodin chocolates ɗin da ya zubar naji tsaiwarsa gefena. Juyowa nayi na kallesa, ya ɗan ɗage min gira alamar kallon fa, ʙoʙarin kauda kaina nayi ya kamoni, a bazata naji saukar sumbata a goshina. Idanuna na lumshe a hankali. Shi kuma ya kai lips ɗinsa kan kunnena a matuʙar low voice ya furta, ā€œYou are beautiful tiger girlā€. Da sauri na buɗe idanun a kansa. Kamar zan yi kuka na ce, ā€œTiger fa?ā€. Ido ɗaya ya kashe min kawai yay gaba batare da ya amsa min ba. Yana buɗe ʙofar nima cikin shagwaɓa na ce, ā€œKaima Lionā€. Wani shegen murmushi kawai ya sakar min batare da yace komai ba ya buɗe ʙofar ya fita abinsa. Nima sai na samu kaina da sakin murmushin har haʙorana na bayyana. Sosai murmushinsa ke sakani farin ciki da nishaɗi. Dan yana bala’in ʙara ʙyau a duk lokacin da yayi sa. A gurguje na ʙarasa gyara ɗakin, nasa turare na fito falo bayan nayi salla. Fes na samu ko’ina anan alamar yasha gyara. Sashen Ummie na nufa ta hanyar da yabi da ni daren jiya. Na jima a can dan yau ma har sai da Mama Balki tace naje gasu Yaya Musaddiq nan zuwa harda Falaq. Cike da farin ciki da zumuɗi na tafin kuwa. Tuni na manta da halin da nake ciki saboda farin cikin ganin Ę“an uwana duk uku. Nan fa na zauna muka buɗe sabuwar hira, har sai da Aunty Falaq ta tsareni naci abinci wai inji Yaya Awwab. Ni saima abin ya ban mamaki. Sai dai ban ja zancen ba na basar dan tunda na shigo na fahimci baya nan. Bayan sun tafi sallar la’asar nace mu shiga muma muyi a bedroom Aunty Falaq taʙi, nayi-nayi da ita tace ALLAH bazata taɓa iya shiga bedroom ɗin Yaya Awwab ba. Zata je sashen su Mama tayo. Sosai nake mamakin yanda suke mugun girmamasa, sai kuma hakan ya birgeni. Tare muka nufi sashen su Maman da ita. Bayan nama guard ɗinsa magana sun kulle sashen. A hanya muka gamu da Hajiya ʙarama ta dawo maybe daga asibiti ne oho mata. Sai dai muna gaisheta sai ga hajiyar nan data ɗakkoni da ga Abuja ta fito a mota itama. Sosai na zuba mata ido, dan tun ranar birthday ɗin nan ban sake ganinta a gidan ba. Itama kallona take kamar wata tsohuwar mayya. Dan haka na tsuke fuska ataʙaice na gaisheta naja hannun Falaq muka wuce. Har muka shige sashen Mama ina jin idanunsu a kammu su duka biyun.. Koda mukai sallar a sashen Mama Balki muka cigaba da zama. Suma su Yaya Musaddiq nan suka samemu. Sabuwar hira muka sake zamanyi yanzu kam harda Mama Balki da mijinta. Sunata bamu labarin Baba muna jin daɗi, sai gab da magriba Hayatu ya shigo yake cewa sun dawo. Yaya Musaddiq yazo suje ya ʙarasa kimtsawa jirginsa na nine ne. Gaba ɗaya kuma duk sai jikinmu yay sanyi, amma babu yanda muka iya tunda cigaba ne yazo mana. Sai kuma munyi haʙuri zamuci ribarsa. Anan mukai sallar magrib ɗin, sannan muka ɗan sake gyara jikinmu dan muma muna son masa rakkiya airport ɗin. Ana kuwa idar da sallar isha’i sai gasu sun dawo. Nasiha sosai Mama Balki da Baba suka sake ma Yaya Musaddiq, sannan muka haɗu mukai masa addu’a. Ya sake kiran su Abba yay musu sallama har nima muka gaisa. Mun fito muka samu har mitsocin da zamu tafi da su airport ɗin an shirya. Da farko nayi mamaki, sai da naga boss ɗin ya fito alamar da shi za’ai rakkiyar sannan na fahimci dalilin shirya motocin da yawa haka. Dan kusan mota biyar. Biyu ta guards ɗin sa. Sai Mama da Baba da Yaya Musaddiq suka shiga ɗaya. Hayatu, Falaq, Hafizzullah suma suka shiga ɗaya. Sai ni da shi a ta tsakkiya duk da ba haka naso ba. Amma Falaq ta turani a motar da tsiya-tsiya tana dariya. Waya yake sanda na shiga, dan haka muna haɗa ido nayi saurin kauda kaina. Sai da mukai nisa da gidan sosai sannan ya kammala wayar, batare dana kallesa ba nace, ā€œIna yiniā€. Bai amsa min ba, sai kaifin idanunsa da nake ji a kaina. Kasa jurewa nayi a hankali na ɗago na ɗan kallesa. Caraf kuwa ya cafke idanun nawa a cikin nasa kamar dama mai jiran hakan. Wani irin kallo yake mun mai tada tsigar jiki da saka jini tsinkewa. Bamma san sanda cikin rawar murya da shagwaɓa na ce masa, ā€œNi ka bar kallonaā€. A hankali ya lumshe idanun ya sake buɗewa, sai kuma ya riʙo hannuna batare da yayi magana ba yanzu ma ya jawoni jikinsa kawai ya rungume. Luff nayi dan nima da alama abinda gangar jikin nawa ke buʙata kenan. Tuna bafa mu kaɗai bane akwai driver ya sani saurin yunʙurin tashi, amma sai ya maidani ya sake matsewa. A marairaice na buɗe baki zanyi magana ya dakatar dani. ā€œBana son surutuā€. A hankali na sauke ajiyar zuciya tare da haɗiye abinda nake son faɗar kuwa. Dan ji nai bazan iya masa musu ba sam. A hakan muka isa airport ina a jikinsa. Munfi tsahon mintuna biyar bayan isowar tamu kuma kafin ya bari muka fita. Jinai gaba ɗaya kunya ta kamani ganin kowa ya fito ashe sai mune kaɗai a mota. Yaya Musaddiq yaja gefe sukai magana. Ban san mi suka tattauna ba dai naga Yayan nata murmushi da kallonmu. Sai kuma ya ɗan sosa kansa kamar wanda yaji kunya. Daga haka kuma naga shima Yaya Musaddiq ɗin yazo yaja Baba da Mama suka koma can. Anan ɗin ma sun ɗan jima, kowa fuskarsa ɗauke da murmushi idan ka cire uban gayyar da shi daman sai yaso yake murmushin. Shiyyasa da wahala ka gane farin cikinsa da akasinsa sai ka masa farin sani na haʙiʙa. Bayan sun gama zantukansu muma munata hirarmu suka dawo inda muke. Baifi mintuna biyar ba aka buʙaci ganin su Yaya a ciki. Tofa ai tuni kuma kuka ya tashi ni da Hafizzullah. Ganin haka itama Aunty Falaq ta fara. Mama Balki da Hayatu na ta mana dariya. Baba ko sai lallashinmu yake, shiko ai kamar ma bai san munayi ba. Haka dai muna ji muna gani Yaya Musaddiq ya wuce ya barmu da kewa. Hafizzullah da Hayatu da Falaq can gida suka wuce. Mu kuma muka nufi gida muma inata mita dan nazata yau a wajenmu muma Hafizzullah ɗin zai kwana. Bai dai tanka min ba har muka isa gida. Hakan ya ʙara tunzurani. Dan haka nama rigashi fita a motar. Badan su Mama Balki dake wajen ba ma da bazanje sashensa ba. Nafi mintina goma da shiga sannan ya shigo. Lokacin har na shiga wanka. Na fito na sameshi zaune a bakin gado yana waya. Wucewa nai cikin closet ɗinsa na shirya. Ina fitowa yana shiga bayin shima. Sai na saka sallaya nayi shafa’i da wutri. Na idar na tashi na fita. A karo na biyu na shiga kitchen ɗin sashensa. Kai tsaye store na shiga na ɗakko catton biyu na bottle water na fito. Bedroom ɗin ba dawo dasu. Har lokacin kuma bai fito ba. Gaba ɗaya na fito da ruwan tare da buɗe musu murfi sai dai ban cire su a jiki ba sannan na ɗauka Alkur’ani na fara karatu. Surorin da duk akace suna karya sihiri nake karantowa ina tofawa a cikin ruwan bayan na ɗaɗɗaga murafan. Nayi nisa sosai a karatun sannan ya fito. Duk da nayi mamakin daɗewar tasa a ciki ban kula ba na cigaba da karatuna a nutse… Sosai karatun nata ke ratsa masa zuciya. Ga yanda zazzaʙar muryarta ke fita cikin nutsuwa da bama komai hakkinsa na wani irin shiga masa har cikin jinin jikinsa. Cikin jin wata irin kasalar dake saukar masa ya ʙarasa closet ɗin sa. Shirin barci yayi shima, ya fito gaban mirror ya saka turare sannan ya ʙarasa saman sofa ya zauna yana satar kallonta ta gefen ido…. Barci nake ji amma tsoron abinda zai iya biyo baya ya hanani tashi naje na kwanta. Koda na kammala addu’oin ma sai na miʙe na kabbara salla. A mamakina sai naga shima ya miʙe ya saka sallaya ya kabbara salar. Mun jima muna miʙama UBANGIJI kukanmu dai sai wajen uku ya katseni cikin bada umarni yace naje na kwanta. Bazan iya masa musu ba. Dan sam banga hayar yin hakan ba a garesa, ga zazzaɓi ya rufeni haka dai na daure naje na kwanta. Duk yanda naso nayi barcin na kasa, sai dai nayi luff a kwancen har ya kammala tashi sabgar yazo ya kwanta. Lokacin da ya sakani a jikinsa wani irin dukan ɗari-ɗari zuciyata ta dinga min, na gama sadaʙarwa yau ma zansha wata azabar sai naji saɓanin haka. Sai ma tadani da yay ya bani maganin zazzaɓi ya sake maidani jikinsa muka kwanta. Babu jimawa kuwa mu duka barci yay awan gaba damu. Koda muka tashi a washe gari babu zazzaɓin, sai dai yanda nake tafiya da ɗan ɗingishi ya sashi min tambaya. Kasa bashi amsa nayi sai idanuna da suka cika da ʙwalla. Shima sai baicedani komai ba ya ʙyaleni kawai yama fita. Kusan ʙarfe goma na idar da sallar walha bayan naje naga Ummie sai gashi ya shigo, kaina a ʙasa na gaidashi, dan rabona da shi tun fita motsa jiki. Kai tsaye yace min ga Doctor tazo dubani. Sosai mamaki ya sani kallonsa, sai dai shi tuni ya ɗauke kansa ma. Ficewa yay abinsa kamar baiga kallon da nake masa ba. A dai-dai nan akai knocking ʙofar, tashi nayi na buɗe, sai ko ga Doctor naci karo da ita. Haka kawai nake jin nauyin matar, dan a haife ta haifi waɗanda ma suka fini, kaina a ʙasa na gaisheta. Yayinda ta amsa min tana kama hannuna muka dawo cikin ɗakin………āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ› (Itama nama ce)

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†_š‘·š’‚š’ˆš’† thirty-one.

    …Ina ji ina gani dole na bar doctor ta dubani, kanta kawai naga tana girgizawa cikin damuwa. Sai dai bata iya cewa komai ba tamun allura da buʙatar ganin Mama Balki. Kaina a ʙasa na bata amsar cewar ba’a nan side take ba. Amma za’a iya kiranta a waya ta bari ya shigo. Babu jimawa kuwa sai gashi ya shigo kamar dama kunnensa a kammu yake. Kallo ɗaya na masa na ɗauke idanuna, sai ma kawai na zame na kwanta abina na juya musu baya. Ina jin lokacin da Doctor ke sanar masa tana buʙatar ganin Mama Balki yace ta sanar masa koma minene ke faruwa karta damu. Ta ɗan jima shiru jimm kafin ta fara masa bayanin daya gama sakani a kunya. Dan bayani ta masa akan lallai ina buʙatar hutu da kulawa. Saboda ciwukan farko basu gama warkewa yanda ya kamata ba. Ga shi kuma an famasu shiyyasa ma nake jin zazzaɓi nake kuma ɗingishi. Badan ma jikina nada ʙyau ba ciwo na saurin warkewa da za’a iya samun matsala. Ta sake tabbatar masa da ina da dauriya, dan ba kowacce mace ke iya ɗaukar irin yanayin ba haka gab-da-gab gaskiya. Ko fargaba da tsotata ya ishi mutum ai. Ta dai jima suna magana da bashi dabarun daya kamata a kula dani domin samun dai-daiton komai yanda ya kamata kuma cikin ʙanʙanin lokaci. Daga haka ta sake bani wasu magungunan ta wuce bayan ta tabbatar masa zata dinga zuwa kullum dubani har na tsawon sati, kuma dan ALLAH na ɗan sami hutu kona satin ne. Koda ta wuce ban iya motsawa ba. Sai dai ina jin kaifin idanunsa a kaina tsahon lokaci kafin ya shige bathroom. Kafin ya fito barci ya kwasheni. Ban tashi farkawa ba sai gab da azhar. Babu kowa a ɗakin sai ɗan short note da naci karo da shi ya ajiye min a gefen fillon da nake kwance. Na jima ina kallon rubutun mai ʙyau kamar ba hannu yayisa ba kafin na saki murmushin daban shirya ba. Na ɗan ji daɗin jikina fiye da yinin jiya dana wuni a ʙuntace, kasancewar su Yaya Musaddiq kawai yasa na dinga dauriya. Wanka na ʙarayi na gyara ɗakin sannan nai zaman cin abincin da yace ɗin, kai tsaye na fahimci Mama Balki ce ta kawosa. Sosai naci na sha magani, sai da nayi salla sannan na tattara kayan abincin na fita zuwa sashen Ummie….

    🪓🪓🪓🪓

    Su amarya Baby an isa ʙasar California lafiya. Sai faman iyayi take da wani yauʙi ita a dole ga amarya. ʘalubale na farko data fara fuskanta a wajen angon nata shine tun a airport ya sakata a taxi wai taje zai ʙaraso. Ya bama mai taxi address ɗin hotel ɗin daya riga yay booking musu tun kafin su iso. Hankalin Baby ya ɗan tashi, amma dai tai ʙoʙarin dannewa tunda yace mata uzirine daya shafesu. Batasha wahala ba kasancewar ta samu mai jiran isowarta cikin ma’aikatan hotel ɗin. Da alama dai mijin nata sananne ne a wajen. Sai ta sake jin kanta ya fasu sama sosai. Wani irin santi da sambatu ta dingayi ganin irin katafaren ɗakin da aka kawota, gashi ya jiʙu da kayan alatu. Dama tun a wajen hotel ɗin take faman sambatu a zuciyarta. Sai da ta gama taɓe-taɓenta da kalle-kalle da santi sannan ta kwanta barcin gajiya, babu batun salla ko duba lokaci, dan a cikin jirgi ko tuna tashi tai salla batayi ba. Yanzu kuma sun sauka maimakon tayi ʙoʙarin ramawa ko’a jikinta. Wankan ma tunda ta shiga tai fitsari taga ta kasa amfani da kayan bathroom ɗin shiyyasa ta haʙura. Tayi nisa a barci sosai aka tasheta. A firgice ya buɗe ido babu addu’a babu komai ta mike zambar tana ʙoʙarin ɓarka ihu. Tsawa ya mata da zabga mata harara da manyan idanunsa. Sosai tsoro ya kamata da ganin yanda duk kamaninsa suka canja. Idanunsa sunyi wani irin jazur kamar ba mijin nata ba. Har ga ALLAH ba wani sonshi take ji ba, kawai kuɗinsa da zigar su Mom yasa ta amince da aurensa. Ta kuma gama shiryama ranta da shawarar ʙawayenta zaman shekara biyu zatayi da shi ta tara abinda ta tara tasa ya saketa ta samu dai-dai da ita yaro mijin wuce sa’a ta aura. Da ʙyar ta danne wata irin tsanarsa da ta sake ji na tsarga mata. Dan komawar idanunsa jajayen nan sai ya sake fito da tsufarsa. Duk da kuwa a fuska ʙyaʙyʙyawane, sai dai ʙaton cikin nan ya masa cikas da tsufa daya fara taso masa. Ɗan murmushi tayi cike da wayancewa da danne abinda ke ranta ta faɗa jikinsa ta rungumesa tana zabga masa kalamai wai tayi missing ɗin sa. Shiru bai rungumeta ba, bai kuma tureta ba, har sai da ta gaji dan kanta ta ɗago. Matsawa yay daga gaban gadon yana ʙoʙarin cire kaya. Da sauri ta kauda fuskarta, dan tulelen cikinsa kamar na mace mai cikin Ę“an uku dake gab da haihuwa. Tas ya gama sannan ya nufi hanyar bayi daga shi sai boxer. Yana gama shigewa ta sauke ajiyar zuciya. Itako taga takanta, wai tayaya zata iya dauriyar bin shawarar ʙawayenta? Tuna burikanta ya sata sauke numfashi. Tana nan zaune abin duniya ya isheta sai gashi ya fito. Yanzu dai towel ne a jikinsa. Zaram ta miʙe tana faɗin, ā€œBara nima nayi wankan to, dama gajiya tasa banyi ba na kwanta kawai ga yunwa kuma ina jiā€. ā€œOkayā€. Kawai yace mata ya cigaba da harkar gabansa. Da ʙyar ta iya samu ta kunna shower tai wankan, cikin son ta birgesa ta fito da ɗan guntun towel. Tako birgesan, dan duk inda tayi biye yake da ita da kallo kamar tsohon maye musamman bayanta. Bayan ta gama shiryawa cikin ʙananun kaya kamar yanda shima ya zuba Ę“ar shara da wando ta dawo kusa da shi ta zauna. Kamar abin arziʙi suka ci abinci tare tana faman masa shagwaɓa ita a dole ga amarya. Sai da yaci yay nak abinsa yay miʙar ʙoshi sannan ya miʙe a wajen. Barci ya ɗan fara figarsa a kujerar tana jikinsa akai kiran wayarsa. Janyeta yay ya tashi ya fita, kusan mintuna goma sai gashi ya dawo.. Da kallo ta dinga binsa, dan abinda aka ɗirka mata sai tsikarinta sukeyi. So take ko ɗan taɓata yayi, amma mutumin nan bashi da wannan niyyar. Ganin fa wankin hula zai kaita dare ga shi tun a yau take son fara tatsar kuɗaɗe dan Mom taci bashi sosai a bikin nan wajen shirya mata ɗaki tana son ta tura a biya kada asirinsu ya tonu. Tashi tai tsam ta nufi gadon da taga yaje ya kwanta. Cike da shagwaɓa ta faɗa masa a jiki. Shiru yay yana kallonta, itako babu kunya babu kawaici ta fara masa abubuwa. Barinta yay tai kiɗanta tai rawarta, kafin shi kuma ya fara maida mata murtani. Abinka da wadda tasha kayan iri-iri harda wanda bai kamata abama amarya irinta farin shiga ba. Gaba ɗaya ta gama sallama masa har bata ma san mi take ba. Hankalinta ya matuʙar gushewa taji kawai yana ɗaɗɗaureta. Da mamaki take kallonsa. Sai ya sakar mata makirin murmushi. Bata iya ta maida masa ba, dan a yanda ya kifata rufda ciki ya ɗaure ɗin ya sokar mata zuciya. Kafin ta samu damar neman ba’asi ya bita ya taushe. Duk da bata wani nutsu tayi islamiyya ba sosai hanyar da mijin nata ke neman bi a jikinta ya matuʙar firgitata. Cikin tashin hankali ta shiga tambayarsa mi yake sonyi haka? Abinda yake son aikatawa fa haramunne, taya zai yi ʙoʙarin mu’amalatar ta ta baya kamar wasu aladu. Ko kallo bata isheshi ba, tana ji tana gani ya aikata saɓon ALLAH da ita, maimakon bin hanyar da ALLAH ya halatta masa yabi wadda ya harta masa. Babu kuma tausayi babu imani sai da yay mata fata-fata. Tun tana kuka da roʙonsa da magiya harta ma suma dan azaba. Gashi ya ɗaureta duka hannayenta da ʙafafu babu damar koda kare kanta ne…..

    ā¤ļøā€šŸ”„āœØā¤ļøā€šŸ”„āœØā¤ļøā€šŸ”„

    A ɓangaren Baba prof koda ya koma gida a jiya yaso bama al’amarin lokaci dan yay nazari, sai dai hakan na neman gagararsa. Washe gari duk da uziririn dake gabansa bai iya fita a gidan ba har kusan sha biyu na rana, dan ya kwana da tunane-tunane ne ya tashi dasu. Wayarsa ya ɗauka har ya danna kiran number Maash sai kuma ya yanke yana mai girgiza kansa. Akalar kiran ya maida kan Hajiya Mammah. Harta tsinke ba’a ɗaga ba wai tana waya. Sake kiran yay dan bazai iya jira harta gama ta kirashi ba. Yanzun ma tana wayar, sai dai kuma tana gab da katsewa aka ɗaga. Cikin bada umarni ya ce, ā€œNafisa ki sameni a gida yanzun nanā€. Daga haka ya katse kiran. Shiru kawai Hajiya Mammah da tun jiya abin duniya ya isa tayi tana bin wayar da kallo. Ita bata motsaba ita bata ajiye ba. A haka kiran Hajiya Rubayya ya shigo mata. Da ʙyar ta iya ɗagawa takai kunnenta. Daga can cikin zumuɗi Hajiya Rubayya ta ce, ā€œMiya faru? Ya kukayi da Baban?ā€. ā€œCa yay na samesa a gida. Ni kuma bana jin zanyi hakan Rubayya. Dan ban san mizan ce da shi ba, kin dai san halin Baba akan ɗan iskan yaron nanā€. ā€œUhm uhm kar kice haka kije. Ai idan kikaʙi zuwa zai ma yarda da abinda ya faɗa kenan. Wannan fa wata gaɓace da zamu kama mu riʙe. Dan ita kawai ta rage mana yanzu. Dan haka tashi kije. Ki kirani ina jin abinda Baba ke faɗa zan dinga faɗa miki amsar da zaki bashiā€. Matuʙar yarda Hajiya Mammah tama Hajiya Rubayya. Dan haka bata kusa ba ta miʙa ta hau shirin tafiya. Ta fito cikin takun nan nata na isa da taʙama sai dai daka ganta kasan ranta a ɓace yake. Gaisheta ma’aikatan gidan keta faman yi cike da girmamawa. Sai dai gaba ɗaya hankalinta ba’a garesu yake ba. Dan dai-dai nan ɗaya daga cikin ʙosassun motocin Maash da ba kasafai yake fita da su ba sai abu mai muhimmanci ta shigo, sai motar guards ɗinsa ɗaya biye da ita. Da farko ta ɗauka Maash ɗinne ya fita yake dawowa, sai da aka buɗe motar taga wanda ya fito a ciki tai tsaiwar sojan badakkare kamar wadda ta suma a tsaye… A hankali black beauty matashin saurayin dogo mai tsananin kammani da su Paah sai dai idanunsa sak irin na Maash ya wani yamutse fuska da bin gidan da kallo. Sam gidan baya wani birgesa a zahirance. Amma acan ʙasan ransa yana jin kewar Ummien sa da son kasancewa da ita. Matsala ɗaya ke masa katanga da yunʙurin zuwa gareta, ɗan uwansa. In har Yayansa na waje komai buʙatar da yake ma wajen shi bazai taɓa iya kasancewa ba. Dan yana jin kamar ya soka masa wuʙa ko ɗaukar bindiga ya harbe masa kai kawai. Sai da ya gama ʙarema gidan kallo batare da hankalinsa ya kai kan Hajiya Mammah ba ya ɗauka side bag ɗinsa irin ta maza matasa masu ji da gayu ya saka. Kansa tsaye babban ʙofar sashen ya nufa, dan sai ya fara zuwa yaga Ummiensa kafin ya ʙarasa sashensa. Yasan dai yanzu su Paah duk basa gida suna office……..āœļø


    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›_*(Itama nama ce)__

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†_š‘·š’‚š’ˆš’† thirty-two

    …..Zaune nake cikin dauriya kan Ummie a saman cinyata ina mata kitso tare da raira karatun Alkur’ani a hankali. Duk da dai Alhamdullah yau ina jin jikina da sauʙi ba kamar jiya ba. Tunda na shigo Mama Balki ta sanar min ai Hafizzullah yazo da safe tare da Hayatu amma sun fita har da Maash sai kawai nace bara nai zaman yima Ummie kitsonta da tun jiya naso yi ALLAH bai ʙaddara ba. Muna fara kitson Mama tace bara taje ta duba su Aunty Falila a kitchen dake girkin rana. Da to na amsa mata na cigaba da kitson ina karatun. Fitar tata baifi da mintuna biyar ba aka buɗe ʙofar ɗakin, sai ban damu ba na cigaba da kitsona ina karatuna da tunanin ko itace ta dawo ɗaukar wani abu. Jin shiru bata ʙaraso ba bata kuma yi magana ba ga wani baʙon ʙamshin turare da ban santa da shi ba yasa na ɗago idanuna na kalla ʙofar. Cak na tsaya da kitson ina bin black beauty matashin saurayin da kallon mamaki kamar yanda shima ya zubamun idanunsa sak irin na Yaya Awwab. Ganin kallon nasa na neman wuce gona da iri fuska a yamutse na ce, ā€œMalam lafiya? Wanene kai? Miya kawoka nan?ā€. Gira ya ɗan ɗage cike da salon iya shege sai kuma ya saki wani faffaɗan murmushi. Hannu ya kai ya ɗan shafi dan tsigigin gemunsa na ɗaukar magana ya wani karkace kai gefe tare da furta, ā€œFAHAD EL-MU’AZZ ADAMS. Kefa ʙyaʙyʙyawa?ā€. Maganarsa ta ʙarshe ta sani ʙin cemasa komai duk da naji wani daɗin jin sunan daya ambata ɗin . Sai ma ɗauke idanun nawa da nai na maida kan Ummie. Takowa yay shima a hankali zuwa inda muke. Zama yay kusa da Ummie ta ɗayan side ɗin, kamar wani ʙaramin yaro ya kwanto jikinta yana mai rungumeta. Cikin rawar marya ya ce, ā€œI miss you mom. I love you with all my heart. You are my world and everything.ā€ sai ga hawaye sharr, sake ʙanʙameta yay sosai a jikinsa. Sosai wani irin tausayinsa ya shiga ratsa min zuciya. Kaina na kauda daga kallonsu nima hawayen na zubo min. Da sauri na share su tare da ʙoʙarin cire kanta a jikina ya ɗago. Da sauri ya ce, ā€œOh oh beauty sai ki tafi kuma? Ki bari na gama da Ummie na zan dawo kankiā€. Harara na zuba masa. Kafin na girgiza kaina da faɗin, ā€œKa kama kanka fa.ā€ Da sauri yako damʙe kan nasa. Sai kuma ya saki murmushi cikin komawa serious saboda hararar dana zabga masa. Hannayensa ya haɗe waje guda. Ya ce, ā€œAm sorry. Barka da rana. Sunana Fahad El-Mu’azz Adams. Autan Ummiensa da Paahā€. Na kula akwaisa da shaʙiyanci, dan haka nayi murmushi da ɗan girgiza kaina. Cikin komawa serious nima nace masa sannu da zuwa. Sai dai yanzu ba kaine autan Ummie ba nice.ā€ Cikin marairaice fuska ya ce, ā€œA’a dan ALLAH kada kimun haka. Na yarda ki zama aunty na kawai. Daga yanzu ma zan na ce dake aunty beautyā€. ā€œDama Auntyn taka ce aiā€.Muka tsinkayi muryar Mama a bayanmu. Da sauri ya juya, sai kuma ya miʙe cike da farin ciki ya nufeta. Babu kunya ya rungumeta. Dariya Mama ta shiga yi da ɗan bubbuga bayansa tana faɗin, ā€œOh ni maigado sai yaushe ne Fahad ɗina zai girma. Haba autan Ummie kafa isa aureā€. ā€œIna ban isa ba Mama. I miss you wlhyā€. ā€œMuma munyi kewarka sosai Fahad. ALLAH yay maka albarka kaji.ā€ ta faɗa tana ɗagosa. Daka gansu kaga waɗanda ke a cikin farin ciki sosai. Cike da girmamawa ya gaisheta, tare da tambayarta jikin Ummie yana mai bin sashen da kallo. Ta amsa masa da kulawa. Kafin ya tambayeta wai wacece ni dan ya matsu ya sani. ʘaramar dariya Mama tayi, tare da faɗin, ā€œA’a bakaji a bakina ba. Ka bari zaka saniā€. Cikin yanayinsa na mutum mai sauʙin kai a yanda na fahimta ni dai ya ce, ā€œOkay Mama ba damuwa. Bari naje nayi wanka sai na dawo ALLAH yasa Ummie ta tashi ta ganni na ganta da ʙyau. Ina fatan kin min farvorite food ɗina dai?ā€. ā€œSasai ma kuwa autan Ummie. Dan har sai kaci ka ture.ā€ Sosai farin cikin sa ya sake bayyana. Ya ɗaga min hannu yana maida bag ɗinsa da faɗin, ā€œBye Aunty beauty ki jirani nazo muyi hira. Dan sai kin faɗa min wacece ke zan barki.ā€ Sosai ya bani dariya. Hakama Mama Balki dariya take yi. Yana gama ficewa na dubi Mama fuskata da sauran dariyar na ce, ā€œMama wannan ɗan naki akwai dai rashin ji a jikinsaā€. Dariya ta sake yi sosai tana kaiwa zaune. Ta ce, ā€œHumm bar Fahad inda kika gansa ya dai so yin barkwancin ne. Amma shima da kike ganinsa wani lokacin akwai miskilancin. Sai dai bai kai Alhaji ʘarami bane kawai. Halinsu ma sam ba iri ɗaya bane ba. Dan shi Fahad na surutu sosai, shiko Alhaji ʙarami maganar ma aiki ce. Nan fa ta shiga bani labarin Fahad da halayensa. Wani nayi mamaki wani nayi dariya wani al’ajabi. Surutunmu ya tada Ummie ma. Tana farkawa ta fara kiran ā€œYunwa Muhammad! Yunwaā€. Aikin kenan yanzu, daga taci abinci sai barci. Idan kaga ta farka yunwar ce ta sake tashinta. Shiyyasa jikinta yake wani irin murjewa tana ʙiba kwarjininta na sake fitowa. Kwana biyu dai Alhmdllh bata wannan bige-bigen. Bamu sani ba ko hakan nada nasaba da canja mata magunguna da akayi ne. Dan a ranar da jikinta ya motsa sosai ina asibiti a yanda Mama ke bani labari anzo da wani baʙon likita tun daga ʙasar RUMAN (Dole mu tuna Shahan-shan namu na IffanšŸ˜˜šŸ˜€). shine ya dubata tare da canja mata allurai da magunguna. Acewarsa a gwada waɗan nan sabin samfir ne da a shekarar nan aka samar dasu akan masu matsalar ʙwaʙwalwa. Ya bada wata ɗaya zai sake dawowa yaga idan an dace. Amma duk da haka a kullum sai doctors daya bari zasu ke kula da ita zasu dinga aika masa da cigaban da ake samu. Sannan ya dakatar da su Hajiya ʙarama da sauran doctors ɗinta a komai acewarsa shi baya haɗa aiki da waɗanda ba wanda yake tare ba. Sosai naso ace sanda abin ya faru ina wajen. Dan ina buʙatar fahimtar yanayin kowa a cikin doctors ɗin nata na baya. Dan nasan ko suna da gaskiya hakan bazai musu daɗi ba. Amma ko yanzu na ɗauki ɗamarar yin hakan…..

    šŸŒ›šŸŒœā£ļøšŸŒ›šŸŒœ

    Ya ALLAHšŸ™ Wanda ke da rabon shiriya a masu ɗakkowa, da masu yaɗawa, da masu jiran a ɗakko su karanta a matsayin bati, ya UBANGIJIN al’ashi. Ya mai RAHAMA da jinʙai. Ya mai fidda rayayye a cikin matacce, ya fidda matacce a cikin rayayye. Nayi tawasalli da sunayenka masu tsarki, waɗanda ka kirayi kanka da su ka kuma sanar damu, da wanda ka barwa kanka saninsu ka keɓancesu gareka. Nayi tawasalli da ɗan gatan nan naka, wanda kace idan muka so shi, mukabi abinda yazo mana da shi na shiriya ka gafarta mana. Ina roʙonka ka shiryar dani da su. Ya rabbi kafisu sanin wahalar da nake sha a yayin rubutun nan. Nakan hana kaina barci domin sauke hakkin masu saya a lokacin da su suke barcin, nakan yini da ciwon kai, ina fama da ciwon idanu, ina fama da ciwon yatsu. Ina fama da ciwon baya. Wataran nakan wayi gari banama jin farin ciki ko sha’awar rubutun, wataran na tashi da uzirin baʙi ko fita. Amma duk nakan kuntata kaina domin naga nayi. Idan har ban kasance na cutar dasu da komai ba a rayuwarsu, ya rabbi! ya rabbi! ya rabbi!! ka shiryar dasu su guji taɓa hakkin daba nasu ba. Ka shiryar dasu su guji ɗaukarma kansu nauyin da zasuyi dana sani a ranar da ake fansa da lada da zunubi. Ya rabbi ka gafarta mana kurakuranmu. Ka shiryar damu, ka nisanta mu ʙuntata zuciyar kowa koda kuwa dabbace. ALLAH kasa mu samu sauʙaʙʙen hisabi batare da an jinkirta mana ba saboda hakkin wasunmu da mukaci a duniya. Dan ALLAH, dan ALLAH. Dan girman ALLAH mu saukaʙama kammu kunji bayin ALLAH. Ni kaɗai nasan a yanayin da nake wannan rubutun musamman a ɗan tsakanin nan, kada ki bari UBANGIJI ya kamaki da laifin hakkina nima bazan so haka ba. Dan bana son akai gaɓar da zan iya tashi tsakkiyar dare domin miʙama UBANGIJINA ʙararki ko ʙararka. Dan ALLAH, dan ALLAH, dan ALLAH. In har da gaske ke masoyiyar MANZON ALLAH ce kina fatan tashi a tawagarsa ranar da kowa ke fatan hakan, idan har da gaske kin yarda da mutuwa da ranar hisabi, idan har kin yadda wannan rubutun hakkina ne ALLAH zai iya cirar min hakkina a jikinki, idan har kin yarda ban taɓa cutar dake da komai ba, idan har kina fatan kema ALLAH ya kiyaye hakkinki ko hakkinka, ku daina ɗakkowa a inda na killacesa, ki daina yaɗawa, kema ki daina karantawa. Wannan itace maganata ta farko kuma ta ʙarshe in sha ALLAHU, ALLAH ya yafe mana kurakuran mu baki ɗaya.šŸ™

    🪓🪓⭐🪓🪓

    Ran Baba prof a ɓace yake kallon Hajiya Mammah dake gaishesa. Bai amsa ba, sai nuna mata agogon dake falon nasa mai shegen ʙyau da ɗaukar hankali yayi. ā€œKalla time, sai yanzu ne kike zuwa bayan tun 12 da wasu mintuna nai kiranki Nafisa?ā€. ā€œKayi haʙuri Baba. Wlhy na fito zan taho sai ga Fahad. Bamma ko tsaya ya ganni ba na taho dan kar kaita jirana. Wlhy duk a tsorace nake, kada su sake ʙoʙarin ʙona mu a cikin gida kamar wancan karon. Ban san wace jaraba ce ta dawo da yaron nan ba ana zaune lafiya.ā€ Ɗan jimmm na wucin gadi ne ya riski Baba prof.. kafin tamkar mai koyon magana ya ce, ā€œWai wane Fahad ɗin?ā€. Cikin rashin damuwa Hajiya Mammah ta ce, ā€œFahad namu mana Baba. Wlhy gashi can ya dawo abinsa. Abinda ma dai ya ɗan bani mamaki shine ganin a motar fitinannen ɗan uwan nasa aka ɗakkosa. Ko sun shirya ne bamu sani ba. Idan ma hakanne ta kasance ai mu abin farin ciki ne a garemu, dan wlhy tsoron tashin hankalin nan nasu nake suzo wataran su ʙonemu ʙurmus mu da gidan kana dai ganin wancan karon da ʙyar muka sha suka so sakamu a tara. Kai ai nikam wannan jini na Ummu-Hidaya ai ba’a cewa komai. Bala’i kala-kala daga wannan sai wancanā€. Yanda Baba prof yay shiru da alama ba fahimtar zantukan Hajiya Mammah yake ba ma shi. Dan sai da ta ɗan kai hannu ta taɓashi sannan ya dawo firgigit. Murmushi yayi zai yi magana dai-dai nan akai knocking ʙofa. Tsaki Hajiya Mammah tayi tana hararar ʙofar dan tasan bai wuce ma’aikatan gidan ba. Cike da wulaʙanci ta bada izinin a shigo. Ilai kuwa cikin ma’aikatan ne. Kansa a ʙasa da girmamawa ya kai durʙushe yana sanarma Baba prof yana da baʙo. Agogo Baba prof ya kalla, cikin ɗan ɓacin rai yace, ā€œBani da apartment da kowa yau, koma su waye a sanar musu suje sa dawo next timeā€. Kai hadimin ya jinjina. Har zai miʙe sai kuma ya koma ya durʙusa. Kansa a ʙasa cikin ɗari-ɗari ya furta, ā€œRanka ya daɗe Commando ne fa, kuma kaine kace ko baka gidan nan yazo nemanka a sanar da kaiā€. Cikin masifa Hajiya Mammah ta juya zata fara danna masa zagi Baba prof ya dakatar da ita. ā€œUhmm Nafisa kinga barshi umarni na ne. Kinga jeki gida kawai idan na gama da shi zan zo na sameki. Komi ke faruwa ki dinga sanar dani ta waya. Sannan kiyi ʙoʙarin Mu’azz da Abdullahi su dawo gida gudun tashin hankali, idan kuma Awwab baya a gidan ki sanarma Mu’azz ya hanashi komawa gani nan zuwa yanzu nimaā€. Maganar yake yana tafiya, dan haka kafin ma ta bashi amsa har ya shige hanyar da zata sadashi da falon baʙi. Galala tai kawai tana kallonsa, can ʙasan ranta mamakin miya rikitashi haka take yi. Tare da mamakin girman wannan baʙo a wajensa. Amma dai koba komai ita hakan yayi mata. Dan ta kuɓuta daga abinda take gudu dai ke nan. Cikin taɓe baki ta miʙe, tare da saɓar handbag ɗinta ta fice hankalinta kwance. Ai garama taje taga show ɗin can gidan, dan babu wasu su Paah da zata kira sai abubuwa sun kankama……….āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›_* _(Itama nama ce)__

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    __š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’† _š‘·š’‚š’ˆš’† thirty-three.

    …Abincin na fara bama Ummie bayan na wanke mata baki da taimakon Mama Balki. Ci kuwa take sosai kamar ko yaushe a kwanakin nan. Lauma biyu uku sai na bata ruwan addu’a ta sha. Ba ruwan addu’ar da nake mata bane kawai, Baba ma na mata, haka akwai wani da Hayatu ya kawo yace daga Sheikh Muhammad bin Khalipha Al-Hussain yake amsowa, tuni kuma ana kawowa masu kula da ita wai ke bata. Dan haka dana tashi sai nake haɗesu waje guda ina bata, kullum kuma Mama Balki kan shafa mata sau uku a jiki, safe, rana da dare idan zata kwanta. Shi kansa Yaya Awwab daga jiya zuwa yau sune ruwan shansa batare daya sani ba. Dan kaf ruwan dake a cikin freight na kwashe na sanya masa na addu’oin a ciki, duk da ina ɗar-ɗar ɗin karya gane wajen buɗe murfin, dan haka nake ta kaf-kaf ɗin bashi ruwa yanzu da kaina. Dawowar Fahad ɗakin ya katse mana shirun da mukayi. Dan yana yin sallama yay tozali da Ummie dake zaune ina bama abinci ya ʙaraso cikin sassarfa ya wani rungumeta har sai da ta saki ʙaramar ʙara tana turesa. Ɗagowa yay cikin tsananin damuwa idanunsa share-share da hawaye yana kallonta. Itama kallon nashi take yi, sai kuma ta kauda kanta tare da zamewa ta kwanta ta juya mana baya. ʘoʙarin komawa side ɗin data juya yayi, amma sai Mama Balki ta dakatar da shi ta hanyar riʙesa. Yayinda ni kuma ʙwallar tausayin ɗa da mahaifiyar suka cika min idanu. Dai-dai nan aka turo ʙofar aka shigo. Tuni ʙamshin turarensa ya wani irin mamaye hancinanmu. Hakan ya samu ɗaga kai mu duka muka kallesa. Shima tsaye yay cak kamar wanda akama umarnin tsayawar. Yayinda Fahad yay wani kalar ɗauke kansa. Mama Balki ce tai ʙarfin halin masa sannu da zuwa. Da ʙyar ya amsa mata yanayinsa na ʙara komawa na ainahin stubborn ɗinsa. A cikin wani irin yanayi mai wahalar fassara batare da ya karaso ba ya juya ya fita abinsa yana jan sirrin tsaki dake bayyana fushinsa. Harara Fahad ya raka bayansa da shi shima yana jan tsakin mai kauri. Sai kuma a hankali ya furta, ā€œMugu kawai azzalumiā€. Har cikin tsakkiyar kaina naji shigar zagin nan. Na ɗan kalla Fahad ɗin naga yanda yake wani cika yana batsewa. Maimakon naji haushinsa sai ya bani tausayi, dan hatta da jijiyoyin kansa duk sun fito raɗa-raɗa haka ma idanunsa sun wani bala’in kaɗawa jazur a ʙanʙanin lokacin nan. Kamar wanda aka tsikara shima ya miʙe zaram. Dai-dai nan Hayatu ya shigo ɗakin da sallama. Cak Fahad ɗin ya tsaya daga yunʙurin fitar da yake yi. Sai kuma murmushi ya ɗan kufce masa, da sauri ya nufi Hayatun yana faɗin, ā€œOyoyo sweet Yayanaā€. Tuni shima Hayatu ya ajiye kayan hannunsa ya buɗe masa hannayensa suka rungume juna. Ajiyar zuciya na sauke a hankali, sai kuma na miʙe batare da nacema kowa komai ba na fita….

    🩸🩸🩸🩸

    Cikin yanayin gajiya ta shigo gidan. Ga damuwar dake a ʙarʙashin zuciyarta a kwanaki biyun nan game da rashin ganin Samraah. Tun a jiya bincikenta ya tabbatar mata da Samraah ce a sashen Awwab dai Hajiya Mammah da bata san an sallamota ba ta gani ba wata ba. Taso sanar ma Yallaɓai amma ta kasa hakan dan tana son ta fara sanin mi bincikensa ya samo masa akan yarinyar. In har wanda zata iya canja ra’ayinsa ne daga kasheta daya ambata sai ta fara shirinta. Idan kuma na wanda bazai iya canja ra’ayin nasa bane nan ma sai ta ɗauki mataki. Dan a wannan gaɓar bazata taɓa bashi goyon baya ba. Tanama Samraah wani irin mahaikacin so mai taɓa zuciya. Ita kaɗai tasan a halin matsanancin kishin da take ciki na Awwab a Ę“an kwanakin nan musamman daga jiya zuwa yau. Babu kowa a falon sai ʙamshi da sanyin ac. Tasan su Arwa sun fita yawonsu, dan Muhseen ne kawai ke zuwa makaranta yanzu a gidan sai Aneesa autar Hajiya Mammah ʙanwar Azizat kenan. Cikin rashin kuzari ta kama ʙarfen upstairs zata fara haura steps ɗin ta tsaya cak. Rawa jikinta ya nema fara yi sakamakon abinda idanunta ke kallo. Cikin wani irin bugawar zuciya da rawar baki ta furta, ā€œFahad!ā€. ā€œYes Ummy. Surpriseā€. Ya faɗa cikin fara’a yana ʙarasowa gareta. Cikin rashin kula da yanayinta ya bata side hug abinsa. Da ʙyar Hajiya ʙarama ta iya jan numfashi da kokarin controlling kanta. Amma ina jikinta karkarwa yake. Dan koda Fahad ya ɗago yana gaisheta sam bama fahimtarsa take ba. Sai da ya ɗan tanʙwaɓeta da zai gittata yana dariya sannan taji abinda yake faɗi na ʙarshe. ā€œOh Ummy mamakin ganina da alama ya sumar dake. Bari naje dai yanzu zan dawo karki faɗama su Azizat na dawoā€. Daga haka yay wucewarsa ya barta a yanayin ʙaulani. Sosai taji fitsarin dake a mararta na ʙoʙarin zubowa. Tuni ta saki handbag ɗinta a wajen ta juya ta fice a falon ʙafafunta na matuʙar rawa. Tana shiga motarta motar Hajiya Mammah na shigowa gidan. Ko bi takanta batayi ba ta wani irin yin reverse da mahaikacin gudu kamar ba’a cikin gida take ba ta fice har tana kusan takama ɗaya a cikin securitys ɗin ʙofar ʙafa ALLAH dai ya taʙaita yaja baya da sauri. Babu wanda ya kawo komai a ransa sai tunanin kiran gaggawa maybe ta samu daga asibiti. Dan sometimes takan yi irin wannan fitar idan hakan ta faru. Sai in ta dawo ta basu haʙuri da sanar musu abinda ya rikita tan. Shiyyasa kowa a gidan ke mata uziri da mata kallon innocent woman dako hannu ka saka mata a baki bazata ciza ba. Wani irin mahaikacin gudu tayi ko’a titin. ALLAH dai ya taʙaita titin anguwa ne. Gashi kuma anguwan masu kuɗi ba wani yawan kai-kawon mutane ake samu ba, motocin ma sai jefi-jefi. Yanzu kam dama rana da wahala ka gani kasancewar duk ana wajen aiki. A cikin ʙanʙanin lokaci ta iso gate ɗin gidan yallaɓai. Horn ta dinga dannawa daya rikita maigadi, jikinsa har rawa yake wajen buɗewa. Ruɗanin da take ciki ya sata mantawa gaba ɗaya yau bata saka niʙaff ba. Sannan kuma da motarta ta amfanin ko yaushe ta shigo gidan bata ɓadda kama ba kamar yanda ta saba. Kasancewar a duka kamanni biyun na baɗini dana zahiri tana da power ɗin shigowa gidan yasa babu wanda yay mamakin ganinta sai dai mamakin yanda ta shigo. To amma idan suka auna da kafin zuwanta wadda tazo zasu iya kallon abin a wani abu daban kuma. A dai-dai ʙofar falon gidan tai parking, ko rufe motarta batayi ba ta afka ciki. Babu kowa a falon, sai tv dake magana ʙasa-ʙasa. Hannunta ta kalla da nufin neman waya, wayam babu handbag. Tunanin ta barta a mota ya sata jan tsaki. Juyawa tai da nufin ɗakko wayar dai-dai nan wanda zata fita ɗakowar dominsa ya fito. Baiyi mamakin ganinta ba, dan yasan zata iya zuwa ɗin dama.. Zaune ta kai dan wata irin hajijiya take ji na neman ɗibarta. Da ʙyar ta iya haɗa kalmar, ā€œFahad ya dawo, yanzu haka yana gidaā€. Zaune ya kai shima a hankali batare daya ce mata komai ba. Sai ma file ɗin hannunsa daya ajiye yana mai dafe kansa da duka hannayensa biyu. Jin shiru baice komai ba ta ɗago ta kallesa. Muryarta har rawa take wajen sake faɗin, ā€œYallaɓai baka ji abinda na faɗa bane?ā€. Wani irin murmushi ya saki, mai bayyanar da tsantsar ɓacin rai da tsufarsa. Ya ce, ā€œNa jiki sarai, shima wanda ke bincike akan yarinyar nan ya kawo sakamakon yanzuā€. Bai gama rufe baki ba ta ɗauki file ɗin ta fara dubawa cikin rawar jiki. Abubuwa masu muhimmanci kawai take dubawa. Abu na farko daya fara jan hankalinta shine cikakken sunan yarinyar. Samraah Abdul-wahab Gwarzo. Na biyu aikin mahaifinta da sanadin rasuwarsa har ma da inda ya rasu. Na ʙarshe MATAR AURE. Rawa bakinta ya fara da ʙyar ta iya haɗa kalmar, ā€œBa…ban fahimci komai ba yallaɓaiā€. Murmushi ya sake saki, sai kuma ya kalleta da idanunsa dake jazur kamar tsohon maciji. Musamman yanda tsufarsa ta sake fitowa fili sai taga har baʙinsa ma ya sake bayyana fiye dana baya mai tsananin shining ɗin hutu. Shima ɗin kallonta yake cikin ido, batare daya janye ba ya furta, ā€œIta ɗin ɗiya ce ga Abdul-wahab Gwarzo (jirgin mota)ā€. Kaɗan ya rage zuciyar Hajiya ʙarama ta ɓaro. Ta wani irin miʙe zambar jikinta na karkarwa tace, ā€œWhat! Jirgin mota? Drivern mahaifin Ummu-Hidaya da kenan?ā€. Kansa kawai ya ɗauke daga kallonta alamar tabbatarwa. Cikin kaushin murya ya cigaba da faɗin, ā€œTabbas nayi kuskuren ʙin bibiyar bayan Abdul-wahab kamar yanda nake biye dana Ibrahim Alonso. Idan baki manta ba nayi hira da yarinya shekara ɗaya data gabata a Kano sakamakon turamin program ɗin bikin buɗe Company da Awwab yayi. Zargin akwai dalilin da yasa ya amsa mata zaiyi hira da ita alhalin bai taɓa yi da ko manyan channels ba yasa na baro India nazo danna tabbatar da ko akwai alaʙa a tsakaninsu. Tako ina bincikena babu ta inda wata alaʙa ta alaʙanta su, dan haka ban maida hankalina ga cikakken sunan yarinyar ba….ā€ ā€œWai kana nufin itace yallaɓai?ā€. Hajiya ʙarama da gaba ɗaya take a gigice ta jeho masa tambaya cikin katsesa. Iska ya furzar mai kauri tare da miʙewa tsaye. Taku ya fara hannayensa duka biyu a goye ya ce, ā€œOf course itace yarinyarā€. ā€œTashin hankali. To amma tayaya tazo Lagos bayan ma’aikaciya ce? Ta yaya kuma Lagos ɗin ma take zaune a Maash Mansion? A ʙarshen zance shine tayi aure bayan fasa aurenta da saurayinta da suka jima a tare. Abin tambayar anan waye ya auretan? Waye kuma yay kidnapping ɗinta kafin auren har sau biyu? Tabbas akwai abinda ya kawota Maash Mansion, minene shi?. Yallaɓai wlhy zan haukace, wane irin ruɗani da tashin hankali ne haka yazo mana a rana ɗaya? Gashi mun gagara magance batun likitocin nan abu sai ʙara nisa yake, duk da dai ba wannan bane kaɗai hope ɗinmu wancan ma zasu iya mana illa tunda ko ganinta bamayi a yanzu balle sanin halin da take cikiā€. Amaimakon amsa mata dukkan tambayoyinta da maganganunta a mugun fusace yay wurgi da ɗan abin deco.. ɗin dake a saman Centre table ɗin gabansu……..āœļø

    *_TypingšŸ“²_*

    *_šŸ›TSUTSAR NAMA….!!šŸ›

    _(Itama nama ce)__

    š‘©š’Šš’š’šš’ š‘Øš’ƒš’…š’–š’š’ š’„š’†šŸ¤™šŸ»

    š‘©š’š’š’Œ š’•š’‰š’“š’†š’†_š‘·š’‚š’ˆš’† thirty-four

    ….Mugun tsorata Hajiya ʙarama tayi har sai da ta rumtse idanunta da toshe kunnenta jikinta na rawa. Shima nashi jikin rawar yake yi na tsantsar ɓacin rai. Kafin ya shiga maimaita kalmar, ā€œDole akwai abinda Awwab ya sani, dole shine ya shirya komai. Ta ya yarinyar dake a Kano zata dawo Lagos? Ta ya ɗiyar Abdul-wahab zata shigo Maash Mansion matsayin Ę“ar aiki? Ta ya?!!! Ta ya?!! Ta yaya?!!!!ā€. Ya faɗa cikin wani irin ʙaraji da ya sake firgita Hajiya ʙarama. Dan bata taɓa ganinsa a irin wannan fushin ba duk da kuwa ita shaidace akan hatsabibancin sa tun ba yanzu ba. Da wani irin fushi ya danna gefen kujerarsa, zuuuu sai ga gurin ya buɗe. Wata Ę“ar loka ce ta bayyana, kwalaben manyan haɗaɗɗun giya masu tsadar gaske suka bayyana. Ɗaya a ciki ya ɗauka, batare da tuna akwai mai amsa suna surukarsa ba a wajen ya ɓalle murfin ya dasa a bakinsa ya shiga kwankwaɗar kayansa. Shike sha, amma Hajiya ʘarama ita ke binsa da kallo kamar tsohuwar mayya. A yanda take jinta yau ɗin nan kamar fa ta amsa itama ta kora. Sai dai kuma tasan hakan zai iya ɓallo mata aiki ne a wajen Paah. Tas ya shanye abinda ke ciki, tare da yin wurgi da kwalbar sannan ya koma cikin kujera yay wata irin lafewa yana sauke numfashi da ʙarfafan ajiyar zuciya tamkar wanda yay wani uban gudu a sahara. Sun kwashi mintuna biyar a haka shiru, kafin ya miʙe batare da ya kalleta ba ya ce, ā€œKije gida zan nemeki.ā€ Baki ta buɗe zatai magana ya ɗaga mata hannu alamar baya son jin komai. Kanta kawai ta jinjina tare da miʙewar ta fice. Da harara ya raka bayanta, yana jin a ransa amfaninta ya kusa ʙarewa a garesa. Juyayyun idanunsa ya maida kan ʙaton hotonsa dake a falon shi da mahaifin Ummie wato Ibrahim. Hoton yay matuʙar ʙyau musamman da suka kasance cikin manyan kaya, su sukansu kuma bakunansu ɗauke da murmushi. Hannayensu riʙe da jariri dake a cikin showal mai tsananin ʙyau da ɗaukar ido. An yi hoton ne a ranar sunan Muhammad Awwab. Shine kuma jinjirin dake a hannun nasu suna kallonsa fuskokinsu ɗauke da murmushi. A fusace ya rarumi ɗayan deco ɗin saman table ɗin ya wulwula sai ko akan hoton. A take gilashin jikinsa ya tsatstsage. Yatsansa ya karkaɗa alamar gargaɗi ma hoton sannan ya wuce fuuuu zuwa bedroom ɗinsa…. A hankali Kukunsa dake laɓe yana kallon komai ya shiga jinjina kansa. Da baya-baya ya koma ya shiga ta cikin store. Stick ya ɗauka cikin dabara ya janye abinda ya kare cctv camaras ɗin dake a kitchen ɗin ta koma yanda take kamar komai bai faru ba. Dan duk leʙen da yay da naɗar abinda ke faruwa a rubuce camara ɗin bata ɗauka ba. Ba yau ya fara hakan ba, domin a ankare yake, ko it kanta camara ɗin babu wanda yasan ya fahimci akwai ta a kitchen ɗin fama cikin gidan baki ɗaya, sai dai bai taɓa cin karo da samun abinda yasan ogansa zaiyi farin ciki ba irin yau, dan koshi kansa a yau ɗin nan ya matuʙar girgiza da shiga mamakin ganin fuskar Hajiya ʙarama a matsayin wadda ta jima tsahon shekaru tana kawoma Baba prof ɗin ziyara amma bai taɓa ganewa ba saboda shigar ɓadda kama da take yi idan zatazo. Ba kuma su taɓa zama a wannan falon sunyi magana ba sai yau ɗin. Aikinsa ya cigaba dayi kamar yanda ya saba….

    šŸ’“ā˜…šŸ’“ā˜…šŸ’“

    A hankali na murɗa handle ɗin ʙofar na tura kamar mai jin tsoron gamo da wani abun firgici. An rage hasken ɗakin ya koma dif sosai. Sai sanyin ac da ʙamshin fresheners dana saka kafin na fita. Ɗan dube-dube na fara kafin idanuna su sauka akansa. Yana can tsaye daga jikin window duka hannayensa goye a bayansa ya ʙurama waje kallo. Cikin sanɗa na ʙarasa shiga ɗakin. Tray ɗin dake hannuna na ɗaura saman Centre table dake a tsakiyar sofas. Kafin na ʙarasa takawa har inda yake cikin sanɗa. Cikin rufe ido da killace duk wata kunya dake cike da zuciyata na ʙarasa ta bayansa a hankali na warware hannayensa dake goye a bayansa na rungumesa ta baya, hannayena zagaye da shafaffen cikinsa. Dan abinka da dogo bawani na iya kai koda kafaɗarsa bane. Data samansa ne ma hannayena bazasu iya kullesa ba saboda yanda ʙirjinsa ke a buɗe alamar motsa jiki. Jikinsa akwai zafi sosai alamar zazzaɓi ko kuma duk ɓacin ran ne oho. Duk da dabaibayin dana masa sam bai motsa ba, na ɗan ciza lips ɗina ina mamakin taurin zuciyarsa. A zahiri kam muryata na maida can ʙasa da Ę“ar shagwaɓa na ce, ā€œMy Lion!ā€. Shiru bai amsa ba. Na ɗan yi jimm kafin na motsa hamnuna na mintsinesa a saman cikinsa kaɗan na sake faɗin, ā€œMy hot! Please answer me ko naita maka kukaā€. Nan ɗin ma kamar bazaice komai ba. Dan kusan fin minti ɗaya kafin naji saukar hannunsa saman nawa. Sosai shima ɗumin hannun nasa ya ratsa min nawa har sai da na ciza lips ɗina kaɗan. A hankali ya jawoni daga bayansa ya maidoni ta gabansa ya tsayar da ni. Har cikin jini da ɓargo na nake jin kaifin idanunsa na ratsani. Dan haka koda kwatance ban iya gwada ɗagowa na kallesa ba. Saukar hannunsa mai ɗumi naji akan haɓata, ya ɗago fuskata sama ta yanda zamu iya ganin juna. Amma sai na lumshe nawa idanun dan bazan iya kallonsa ba. Yafi minti ɗaya yana ʙarema fuskar tawa kallo, ina jin hakanne ta hanyar kaifi da tasirin ʙarfin idanunsa a kaina. Da wani irin ʙyar, tamkar wanda akama dole cikin maʙoshi ya furta, ā€œMi kike buʙata?ā€. Sai da na ʙara runtse idanuna da ʙyau kafin na ɗaga hannuna na ɗaura yatsana manuniya akan jikinsa alamar shi. Ina ji ya ɗan furzar da numfashi mai ɗan sauti kafin ya furta, ā€œOpen your eyesā€. Kafaɗa na maʙe masa da faɗin, ā€œUhm-uhmmm!ā€. Cikin shagwaɓa. ā€œWhy?ā€. ā€œIna jin kunyan kaā€. ā€œWhat is kunya?ā€.Bamma san sanda na ware duk girman idanuna ba a kansa. Cikin suɓutar baki na ce, ā€œBama ka sanshi ba?ā€. Kansa ya jinjina min kawai idanunsa da gaba ɗaya suka canja launi a cikin nawa, ya wani ʙankancesu da shanyesu sun koma wasu luu-luu da su tamkar mai son yin barci. Kasa jurewa nayi, na rissinar da nawa idanun a hankali ina maida fuskata ʙasa. Sai kuma na ɗaura bayan hannuna akan hannunsa da har yanzu ke akan haɓata. ā€œYaya jikinka fa zafi, baka da lafiya ne?ā€. Shiru kamar bazai amsa ni ba, sai kuma ya jawoni jikinsa a hankali ya rungume. Da ʙarfi na sauke ajiyar zuciya, dan wani ratsani zafin jikin nasa yayi har cikin ʙashi. Cikin kasa daurewa na sake faɗin, ā€œALLAH baka da lafiya. Please muje kasha maganiā€. ā€œNooh!ā€. Ya faɗa da ɗan kaushin murya yana sake ʙanʙameni. Tuno maganar Mama nayi da tace baya ʙaunar magani. Sai naji abin ya bani dariya ma. Namiji da shi babba amma yake tsoron magani. Mun jima tsaye a haka kafin na ɗago dan ʙafafuna sun fara gajiya. Cikin raunin murya kamar zanyi kuka nace, ā€œALLAH yaya ʙafafuna sun gaji ni daiā€. Baice komai ba, baima da alamar motsawa. Sai da ya mula dan kansa kafin ya ɗagoni. Ajiyar zuciya na sauke. A saman sofa ya kawoni ya zaunar, shi kuma ya wuce closet. Da kallo kawai na bisa ina mai sauke ajiyar zuciya. Sosai tausayinsu ya kamani shi da ɗan uwan nasa. Dan a kallo ɗaya zaka iya fahimtar tsantsar ʙiyayyar da sukema juna a bayyane take. Nayi nisa sosai a tunani har ya dawo ban sani ba. Sai da ya kama min hannu na dawo firgigit tare da ɗagowa na kallesa. Da sauri na kauda kaina, dan bathrobe ce a jikinsa blue black bai ko ɗaure igiyoyin ba, hakkan ya bama boxer ɗinsa damar bayyana da murɗaɗɗen jikinsa. Magana na buɗe baki zanyi yay min alamar zipping akan lips. Dole na haɗiye sai dai zuciyata sai faman dukan uku-uku take. Tsorona kar yace wanka zan masa. Wani wawan ajiyar zuciya na sauke ganin saɓanin hakan. Dan ʙofa ya buɗe muka fito, sai kuma na shiga wasi-wasin ina zamuje haka. Bamu fita ba a ta wajen bedroom ɗin nasa ya buɗe ʙofar da na daɗe ina tunanin ta bedroom ce itama, ashe ba haka bane. Dan gani nai kawai mun fito ta wani ʙyaʙyʙyawan waje da ʙaton swimming pool ne kawai a cikinsa. A yanayin kamar a ɗaki, sai dai ta saman ginin kana iya hango sararin samaniya, hakama ta jikin bango zallar gilashi ne da kake iya hango cikin garden ɗin nan. Ata ʙasa an matuʙar ʙawatashi da green carpet tamkar koriyar ciyawa farkon toho. Sai hakan ya bada wani irin ʙawa musamman da yanayin ruwan shi kuma ya kasance blue yana wani walʙiya da ʙyalli kamar kaci da haʙori. Sosai dogayen fararen kujerun da kallo ɗaya zakama tausasan katifun samansu kasan zasuyi laushi suka sake ɗaukar hankalina. Na shagala matuʙa da kallon wajen har ban san ma ya zame bathrobe ɗin jikin nasa ba. Sai da ya rungumeni ta baya sannan na ja ajiyar zuciya. Yanda yake mun numfashi ata bayan kunne yay matuʙar saka tsigar jikina ta shi. Bamma san na ʙanʙame hannunsa dake saman cikina ba ina ʙara manne bayana da jikinsa idanuna a rufe. Cikin soft and silent voice ɗin shin nan yana wani irin mun salo a cikin kunne ya furta, ā€œZa kiyi wanka a ciki?ā€. Sosai na ʙara ʙanʙame jikina ina jujjuya masa kaina dake a saman ʙirjinsa. ā€œWhy?ā€. Ya faɗa yanayi kamar zai ciza kunnena. Jinai jikina yana neman fara rawa. Lips ɗina na rawa na ce, ā€œYaya wlhy tsoro nake ji. Ban taɓa shiga ruwa ba irin hakaā€. Komai baice min ba, sai ɗan kwalina daya zame yana ʙoʙarin cusa hannunsa cikin gashin. Tanan kuma ɗayan hannunsa na yawo a jikina. Cikin ɗan ʙarfin da ya rage mun da sauri na janye jikin nawa dake ʙoʙarin fara rawa ina sauke numfashi da sauri-sauri. Komai baice da ni ba, bai kuma kallan ba, sai ʙarasa sakimmin hannun da yay a hankali. Idanuna na runtse, kusan minti ɗaya na buɗe su da sauri saboda jin ʙarar faɗawarsa cikin ruwan. Waro idanuwan nayi sosai ganin yanda ya wani nutse can ʙasa gaba ɗayansa sai motsin ruwan kawai kake gani ta sama…….āœļø35🄱 wazai tafo mana Please

    15 Comments

    Heads up! Your comment will be invisible to other guests and subscribers (except for replies), including you after a grace period.
    1. Farida Bello
      Jun 4, '24 at 11:17 am

      Tnx

      1. Abdul
        Author
        @Farida BelloJun 4, '24 at 12:01 pm

        idan wani littafi sai kumana magana

        1. Khadija Muhammad
          @AbdulJun 8, '24 at 12:11 pm

          Allah ya saka da alkhairi ameen.. sannan muna cigiyan wasu littattafai yanci da rayuwa, bakon munafiki da masarauta Allah yasa akwai

          1. Abdul
            Author
            @Khadija MuhammadJun 8, '24 at 1:02 pm

            su kike bukata kina a cikin a group din ma na Whastapp

    2. Ummulkhair Sani
      Jun 4, '24 at 5:28 pm

      Barka da kokari, so interesting novel, amma don Allah ba a Gama book din bane complete

      1. Abdul
        Author
        @Ummulkhair SaniJun 4, '24 at 5:44 pm

        eh har yanzu ba’a gama ba

        1. Sumayya Ishaq
          @AbdulJun 21, '24 at 1:28 pm

          Tsutsar nama book 3 page fifty six

        2. Bilkisu umar Usman
          @AbdulJun 30, '24 at 4:21 am

          Masha allahu alhamdulilah

      2. Hafsat Sheriff
        @Ummulkhair SaniAug 1, '24 at 4:42 pm

        Thanks,Amma yaushe za’ayi sauran

    3. Khadija Muhammad
      Jun 13, '24 at 5:59 am

      Ahah.
      A ina zanga link din?

      1. Abdul
        Author
        @Khadija MuhammadJun 13, '24 at 10:25 am

        https://chat.whatsapp.com/Gbut9ibvwWM8JPk0qoMEiZ wannan shine group din mu na WhatsApp

        1. Hauwau Muhammed
          @AbdulJul 3, '24 at 9:49 pm

          Tsutsar nama babu complete ne dun Allah a taimaka mana da sauran. Thank you

    4. fatima Abubakar
      Jun 28, '24 at 5:18 am

      Barka da qoqari

    5. fatima umar
      Jul 14, '24 at 10:52 pm

      assalamu alaikum cigavan tsutsar nama book3

      1. Abdul
        Author
        @fatima umarJul 18, '24 at 10:24 am

        ai bata gama ba

    Note
    error: Content is protected !!