[19/09, 1:04 pm] Sadiya Abdulrazak: *KU YI MANA ADALCI* NA Sadiya Abdulrazak Page 1 Marubuciyar Aure A Yau Sandar dukan uwargida Ranar Kuka Miji goma Zuciyar mace Iya ruwa Wani auren Da Walakin Wutar Ƙaiƙayi Matar shige. Dss Duniya juyi-juyi, kawaɗo ya faɗa a ruwan zafi, ina yawan tunawa da wannan karin maganar cikin zuciyata, saboda a yanzu dai yana taka ta shi rawar a cikin rayuwar aurena. A baya idan wani ya ce mini zan iya yin bacci ba a kwance a ƙirjin mijina ba alhalin muna kwance a gado ɗaya, zan shiga shakkun tabbatuwar hakan, inda a ce wani ya taɓa faɗa mini akwai ranar da za ta zo muna gida ɗaya da mijina mu raba ɗaki kowa ya kwana shi kaɗai a na shi ɗakin wallahi nan take zan daka tsalle na musa cikin isa, amma sai ga shi zamani ya jujjuya da rayuwar aurenmu ya watso mu ƙadamin da muke ciki a yau, wanda ya fi kama da rayuwar maƙiya ba masoya ba. Juyi na yi a makeken gadon nawa, na lalubo filo na rungume, ina sane da hasken wayata da yake ta kawowa a karo na babu adadi, alamun mai kiran wayar har yanzu bai gajiya ba, na mirgina na kalli wayar, ba don neman sanin mai kiran ba, don na san wannan, agogon wayar na duba wanda ya nuna ƙarfe sha biyu na dare da minti goma, idan na yi rantsuwa ba zan yi kaffara ba, sai yanzu Sadam ya gama waya da chatting ɗinsa da matan da yake ganin sun fi ni daraja a halin yanzu, wanda nake ƙarfafa zargin sun kunna shi ne, yake neman yadda zai kashe wannan wutar ta wajena, don haka na ƙudure ba zan iya amsa kiransa ba, duk da ban manta da hukuncin matar da mijinta ya kira ta shimfiɗarsa ta ƙi amsa kira ba. Ina sane ƙofar ɗakina a buɗe take, don haka shigowarsa ba ta ba ni tsoro ba, amma ta ba ni mamaki, nan take na tuna da rantsuwar da ya taɓa yi mini a ranar da nake kuka ina tabbatar masa ba zan sake kwana a ɗakinsa ba, ya ce"Na rantse da Allah Sayyada babu macen da ta isa na bi ta ɗakinta na kwana da ita, kuma tun da ni mijinki dole ki amsa kirana a duk lokacin da na buƙaci hakan". Shin na karya masa rantsuwarsa ne tun ba a je ko'ina ba? Lumshe ido na yi kamar mai bacci, daidai lokacin da ya kai hannu ya kunna globe ɗin ɗakin, ya taka a hankali ya ƙaraso ya zauna a gefen gadon "Sayyada, Sayyada". Ya shiga kirana da taushin murya kamar munafiki, ban ko motsa ba, don haka ya kai hannu ya fara taɓa fuskanta, na janye hannun na shi da sauri tamkar wanda ya taɓa ni da bakin wuta, ya riƙe hannun nawa ƙam ya jijjiga shi sannan ya ce"Tashi mana, ina ta kiran wayarki ashe kin yi bacci". Na fizge hannun na ce"Ban yi bacci ba, zuwa ne ba zan yi ba! Kenan ba ka yarda ba da na ce maka ba zan sake kwana a ɗakinka ba ko?" Ya sauke numfashi, har yanzu da wannan sanyin muryar wanda yake yaudarata da shi a da, ya ce"Haba Sayyada, na zata wannan ya wuce ai". Na ce"Ba zai wuce ba har abada". Ya ce"Yaushe kika koyi gardama ne? Yaushe kika koyi musu da ni?" Kamar zan yi kuka na ce"Tun ranar da ka nuna mini matsayi da darajata sun ɓare a wajenka". Tsaki ya ja, a wannan karon sai ya canza murya ya kaurara ta ya ce"Dalla tashi ki wuce mu je". Na yi banza da shi, zuciyata ta fara yi mini zafi, ina tuna miyagun kalamansa a kaina. "Ki tashi mu je ki ba ni hakkina Malama!" Ya maimaita mini cikin daka tsawa. Ni ma ɗin a tsawace kuma cikin kuka na ce"Ba zan bayar ba! Na ƙarfi ne". Ya tashi tsaye yana ce"To ai ina da ƙarfin". Ƙarfin kuwa ya saka ya fizgo ni daga gadon, abinka da 'yar ƙarama mai ƙaramin jiki ba tsayi ba ƙiba, shi kuma dogo mai ƙiba ƙaƙƙarfa, nan take ya ɗauke ni cak, duk shure-shuren da nake yi da dukansa bai sare ba har sai da ya dangana ni da gadon ɗakinsa, irin abin da ya faru a daren da na ce ba zan sake shiga ɗakinsa ba shi ne ya faru a yau ma, fyaɗe Sadam ya yi mini karo na biyu a tsayin zaman aurenmu, duk miyagun kalaman da na dinga jifansa da su ba su saka ya sare ba, har sai da ya kai inda yake son zuwa, na yi laƙwas a gadon ina kuka mai sauti, irin mai cin rai ɗin nan, na yi mai isa ta babu mai rarrashi, sanda na taƙaita na rarrashi kaina kuwa shi tuni ya yi bacci, na kalle shi ta hasken ɗakin, baƙi ne mummuna, amma a yanzu na gane hakan, domin kuwa a shekarun baya kafin zamanmu ya hargitse wallahi gani nake yi ko gasar kyau Sadam ya shiga zai iya shiga sahun farko-farko, ashe soyayya tana ɓoye muni? Tirr! Ni Sayyada na la'anci kalmar soyayya da masu bauta mata indai a haka ƙarshenta yake ƙarewa kowa. Na daɗe kwance a haka hawaye yana gangara ta gefen idona, ji nake zuciyata ta yi mini nauyin da nake jin kamar babu macen da ta fi ni shiga ƙunci, a hankali na yunƙura na tashi, na ɗauki yaloluwar rigar baccina da ya yaga rabinta na bar ɗakin. Bayan na yi wanka na kwanta sai na fara jin ciwon kai kaɗan-kaɗan, tsallen da na yi na afka kogin tunani kuwa ya ta'azzara hauhawar farashin ciwon kan, wanda dama tuni ya zame min jiki. Sautin kiran sallar farko da ya karaɗe unguwar ne ya ankarar da ni tabbas yau na kwana ban runtsa ba, idan aka cire baccin da na samu tsakanin bayan sallar isha'i zuwa ƙarfe goma da dawowar Sadam ɗin ta tashe ni, sai da na yi sallar asuba sannan bacci ya ɗauke ni a kan sallayar. Sai wajen ƙarfe tara na tashi, na yi wanka na saka doguwar rigar leshi na faɗa kitchen, a raina ina addu'ar Allah Ya sa bai fita ba, ruwan shayi kawai na dafa, na ɗakko biredi da bota na ajiye a dining, na haɗa nawa shayin na koma falo na zauna ina sha. Ban yi nisa da fara sha ba ƙamshin turarensa ya cika hancina, hakan ya tabbatar mini da fitowarsa, na juya a hankali na kalle shi, fes yake fuskarsa da walwala alamar bai tashi da wata damuwa ba, ina kallon shi muka haɗa ido, ya sakar mini murmushi ya ce"Morning". Duk yadda na so na mayar masa murmushin na kasa yi ko da kuwa na gefen baki, amma dai na amsa masa da faɗin"Morning". Sannan na tashi na ƙarasa dining ɗin, ya zauna, ni kuma na tsaya na haɗa masa shayin na tura masa gabansa, zan bar wajen ya riƙo hannuna ya ce"Idonki ya kumbura, sorry". Na gyaɗa masa kai alamar na ji, sannan na zame hannun na koma ɗakina, mayafi da jaka na ɗauka na saka wayata a ciki, na zura takalmi, na dawo falon na zauna, ina jira ya gama na ji yadda za mu kwashe, duk tunanin da na kwana ina yi jiya mafita ɗaya na samu a kan burin gyaran rayuwata, shi ne na ziyarci asibiti a yau na fara gyara kuskurena, don a yanzu shi ne kuskuren da ya fi damuna kuma ƙarami cikin kura-kuran da na aikata. Yana gamawa ya zo ya saka kai zai bar falon, bayan ya yi mini kallo ɗaya, na tashi da sauri na bi bayansa, tun da na lura hauka yake son manna mini, ai dai ya sani gari banza ba zan saka mayafi da takalmi har ma da jaka don na ji daɗin zaman falo ba. "Amma dai ka san ba haka kawai na saka mayafi ba ko?" Na faɗa a gadarance. Ya yi tsaki ya ce"Allah wadaran naka ya lalace, na ga ranar da za ki iya magana da miji ke dai". 'Idan ya zama dole sai na kira ka da miji to dole na ƙara da faɗin mijin ƙaddara' Na faɗa a raina, a fili kuma kau da kai na yi ƙwalla tana kawo idona na ce"Ka sauke ni a asibiti". "Ba ki da lafiya ne?" Ya tambaya hankalinsa na kan wayarsa da ya ciro daga aljihu. Na ce"E, ba ni da lafiya". Ya ce"Mene ne yake damunki?" Na ce"Tsakanina da likata ne". Ya ce"Ok, idan na fita zan turo likita sai ki yi masa bayani". Na ce"Asibitin nake son zuwa". Kai tsaye ya ce"Ba za ki je ba". Da sauri na sha gabansa a harzuƙe na ce"Na gaji! Na gaji da wannan mulkin mallakar da kake yi mini, na gaji da yadda kake tauye ni, ba zan zuba ido ka kashe min rayuwa ba fa, na gaji da zama babu haihuwa, ina son ganin jinina, don na gane a yanzu su ne gatana kuma abun ɗebe kewa ba kai ba!" Na rushe da kuka ina tuna girman kuskuren da na yi na biye wa namiji cikin guguwar soyayya, wacce ba ta juye ni a ko'ina ba sai cikin karmamaki. Tsaki ya yi, ya raɓe ni zai wuce, ai kuwa na daka tsalle na tsaya a gabansa ina cewa"Ya zama dole na haihu Saddam, ya zama dole ka je ka ƙaryata cewar ni juya a idon duniya, ko da kuwa ba za ka fasa ƙara aure ba". Da sigar rainin hankali ya ce"To kin tanadi loud speaker da zan yi sanarwar?" Takaici ya sa na ji kamar na zage shi tass, amma na kasa, ina sane mijina ne, ina sane ina yi masa kalaman da ba su kamata ba, ni dai har na fara tunanin ko da aka ce mata sun fi maza yawa a wuta, to silar mazan mata za su kasance a wuta. Ina yi masa wannan kallon na tsantsar takaici ya fice daga falon yana cewa"Na aiko likitan ko dama rashin lafiyan naki na manufa ne?" Na ce"Ba na so, kar ka aiko min kowa, ni zan yanke nawa hukuncin". Ya ɗaga murya ya ce"To idan kin tashi yanke shi hukuncin ki wasa wuƙar". Ina kallon shi har ya shiga motarsa, waya kare a kunnensa, mai gadi ya buɗe masa gate ya bar gidan. Da baya da baya na koma na zauna a kujera, na fashe da kuka, kukan kewa, ina kewar haihuwa da son ganin yarana, a wannan karon na shirya fito na fito da Sadam indai a kan haihuwa ne, ko ya bar ni na haihu ko kuma na haƙura da auren bakiɗaya, ai ana cewa mace ta yi haƙuri ta jure baƙinciki namiji ne saboda tunanin makomar yaranta, to ni kuma babu yaran ballantana na ce zamansu nake yi, na kai kamar minti ashirin a zaune kafin na tashi, na ɗauki jakar tawa na share hawaye na kama hanyar fita tsakar gidan, a bakin gate din na tsaya na gaishe da dattijon mai gadin, ya amsa yana mayar min da gaisuwar,ganin ba shi da niyyar yunƙurawa ta buɗe min yasa na ce"Baba zan fita ne". Ya ɗan diririce kafin ya ce"A! Amma...Hajiya cikin girmamawa nake sanar da ke cewar Alhaji ya ce kar na sake bari ki fita, ki yi haƙuri, a gafarce ni,umarni ne daga sama". Na ce"Don Allah ka buɗe min, ba ni da lafiya ne, asibiti zan je, kuma ba zan bari ya ga laifinka ba wallahi". Cikin damuwa ya ce"A dai yi haƙuri Hajiya, a kan aikina nake". Huci kawai na yi na juya na koma cikin gidan da gudu, kitchen na nufa don na gama yanke hukuncin da nake ganin shi ne mafitata a halin yanzu, wuƙa na zaro sabuwa dal na cire ta daga gidanta, zuciya tana ƙara zuga ni da ingiza ni na aikata kawai, tare da gudunmawar tunawa da irin tauye ni ɗin da aka yi aka cutar da ni, don haka na ji dole na ƙwatarwa kaina 'yanci. 08028966015 [20/09, 5:22 pm] Sadiya Abdulrazak: *KU YI MANA ADALCI* NA Sadiya Abdulrazak Page 1 Buɗe damtsen hannuna na yi, na ajiye wuƙar na fara matsa hannun nawa don jin yadda zaman implant ɗin yake, na ci alwashin yau ba zai kwana a hannuna ba, ko da kuwa zan mutu ne wajen azabar cire shi, na ɗora wuƙar a daidai wajen zan yanka hannun, tsoro da tausayi kaina suka kama ni, zuciyata ta ce mini 'A'a fa Sayyada wannan kasada ce, idan kika yanka kanki jini ya ɓalle miki komai zai iya faruwa, ƙila azaba ta sa ki kasa fita daga ɗakin ma ballantana ki nemi agajin Baba mai gadi, shikenan sai ki mutu a banza burin Sadam ya cika, ya ji daɗin auren shi'. Wata zuciyar kuma ta shiga zuga ni da faɗin'Babu abin da zai faru, ki daure kawai ki yanka ki zare tsinke, ya zo ya same miki cikin jini dole hankalinsa zai tashi ya san tura ta kai ki bango, ƙila silar haka ya fara yi miki adalci. Na dawo falo na zauna da wuƙar a hannu, na yi zuru ina tunanin na yi ko kar na yi? Na san dole akwai zafi, kuma yanzu safiya ce, awa nawa zan yi a cikin azabar nan? Sai dab da magriba yake dawowa fa, na daɗe ina ƙullawa da kuncewa kafin na bar shi a kan zan yanka ɗin, amma sai na ji dawowar shi gidan, yadda ba zan sha wuya sosai ba, da haka na mayar da wuƙar, na fara gyaran gidan, na gama na nemi waje na kwanta ina ta tunanin rayuwa, zuciyata cike da kewa, sai a yanzu ne da Sadam ya canza min hali ya juya min baya kaɗaici yake damuna, kaɗaicin haihuwa da na abokin shawara ko ƙawa. Wayata na ɗakko na kira mahaifiyata muka gaisa, mun jima muna fira, amma na kasa faɗa mata damuwata, na san idan na faɗa mata planing na yi a duk tsayin shekaru ukun nan da aurenmu ya yi, shi yasa ban samu ciki ba za ta ga laifina sosai, kuma za ta yi min faɗa, musamman ganin yadda ta fi kowa nuna damuwa a kan rashin samun cikina, bayan mun gama na kira Babana, shi ma suka gaisa, sannan na kira ƙanwata Salma ita ma mun daɗe muna fira, ita dai Salma kamar ita ta tsarawa kanta, ba ta da wata matsala a gidan aurenta, kullum cikin yabon mijinta take yi, ga kuma ɗansu mai shekara ɗaya abun sha'awa, daga nan na kira Anisa, ƙawata kuma 'yar'uwarta, yau sai na ji kamar na bayyana mata damuwata, da kuma abin da nake shirin aikatawa ko za ta ba ta shawara, amma kuma ba na son a ga laifinta, don ni kaina sai yanzu nake raina wayona, na yi nadamar biyewa daɗin bakin namiji, kodayake umarni ma zan ce, tun da a lokacin ba na iya tsallake umarninsa shiyasa na amince da tsarinsa. Ƙalau na gabatar da wunin ranar, na yi girki da yamma na ci, amma iya cikina, dab da zai dawo gidan na ɗakko wuƙar na zo falo na zauna, har da saka riga mara hannu don na ji daɗin gabatar da aikina, idan na tuna azabar da zan yi wa kaina sai hawaye ya ƙwace min, dab da magriba na ji ƙarar buɗe masa gate, na ɗauki wuƙar da sauri na runtse ido zuciya na ƙara zuga ni, na luma ta a daidai saman inda tsinken yake na yanka da ƙarfi, nan take kuwa na saki wuƙar ta faɗi, na ƙwalla ƙarar azaba ina fashewa da kuka, babu jira jini ya wanke min hannu, duk yadda na so na zaro tsinken haƙura na yi, saboda zafin da nake ji ba zai bari na taɓa wajen yankan ba, kwanciya na yi a wajen ina kuka riƙe da hannun. Shi kuma kamar ya san tana neman taimakonsa, ya nemi waje ya zauna a baranda, Safna ta kira shi yana hanya ya ce mata idan ya ƙarasa zai kira ta, Safna ƙawarsa ce wacce ita ta maye gurbin Sayyada a yanzu ta fannin neman shawara da tattauna muhimman batutuwa, uwa-uba kuma matar da zai aura, sun shaƙu sosai, a asibitin da take aiki suka haɗu, lokacin ya shiga ganin likita, yanzu ma fira kawai suke yi tana jaddada masa yau a gidansu zai ci abincin dare, ya tabbatar mata da zai halarta, daga nan suka cigaba da fira. Ina can kwance ina kukan azaba, shiru bai shigo ɗakin ba, ga shi ba na so ya gane ina nadamar yanka hannun nawa ballantana neman taimakonsa, sai da ya gama wayarsa a tsanake ya shigo ɗakin, kukana ne ya fara sauka a kunnensa, kafin ya gan ni riƙe da hannu jikina ya wanke da jini, zuciyarsa ta doka, ya saki wayar hannunsa da sauri ya ƙarasa inda nake yana cewa"Sayyada! Ke mene ne ya same ki?" Ban ce komai ba sai kukana da ya tsananta, yana ganin wuƙar tsoro ya ƙara kama shi, da ƙarfi ya ce"Me ya same ki!? Kar ki ce mini yanka hannunki kika yi". Cikin kuka na ce"Na gaji, wallahi yau ba zan kwana da tsinken cutarwar nan a jikina ba, cire shi zan yi, ko da zan mutu, indai kai a tsarinka ba ka son haihuwa da ni har abada to sai dai yau ka sake ni, na gama planing har abada". Na kai hannu zan ɗauki wuƙar, ya riga ni ɗauka, duk ya firgice ya ce"Kin fara shaye-shaye ne Sayyada? Ko taɓin hankali kika samu?" Duk da a raina na san ƙarya nake yi ba iya sake saka wuƙar zan yi a jikina ba, amma haka na daure na yunƙura da nufin ƙwacewa ina cewa"Ka ba ni! Ka ba ni na ƙarasa aikina Sadam, kuma ka sake ni na gaji da zama da kai". A raunane ya ce"Ki yi haƙuri don Allah, mu ke na kai ki asibiti, jininki yana ta zuba fa". Da ƙarfin hali na ce"Babu inda zan je, na fi so na mutu". Ya rasa ma ta ina zai fara, ya tuna idan ya kaita asibiti za a zargi wani abu, don haka ya kira likitansu a waya ya sanar da shi abin da yake faruwa, ya ce ya kawo ta asibitin shi yanzu zai je ya same su, ya ajiye wayar yana cewa"Sayyada tashi mu je asibiti kin ji, za a cire miki shikenan". Da ƙyar ya lallaɓa ni na yarda mu je asibitin, sai da na ga ran shi ya fara ɓaci, na ji tsoron ya yi zuciya ya rabu da ni, a mota muna tafiya yake cewa"Haba Sayyada ba ki kyauta min ba sam, wannan ai kin tona mana asiri, me yasa ba za ki faɗa min ke dole kin gaji da planing ɗin ba?" Takaici kamar na buge bakinsa, da wane yaren yake nufin na nuna masa gajiyawata ya gane idan ba wannan fa na yi yanzu ba? Ban ce komai ba har muka ƙarasa asibitin, da yake asibiti ne mai zaman kansa kuma yana da hanya nan take aka shiga ba ni taimako ba tare da bin diddigin abin da ya faru ba. Likitan sai nasiha yake mini bayan an gama yi mini ɗinkin, ina ta hawaye, ya saka min ruwa, ya kalli Sadam ya ce"Zan yi mata allurar da za ta samu bacci". Ya ce"Don Allah mu je gida ka yi mata". Ya ce"A'a ba zan sallame ta a yau ba fa, a ƙalla ta yi kwana uku sai ku koma gidan na cigaba da zuwa ina duba ta, amma yanzu dai ba zan yarda ku tafi gida ba, kuma yana da kyau ta yi bacci". Sadam ya shiga damuwa, ya ce"To tsaya mu yi magana da ita kafin allurar, la ba mu waje don Allah". "Ok" kawai ya ce ya bar ɗakin. Ya zauna a gefen gadon yana kallona, kallon ma na kasa fassara shi, amma kamar ba na tausayi ba ne, sai dai kuma fuskarsa babu ɓacin rai sosai, ya ce"Amma wallahi ke daƙiƙiya ce, ban da hauka ta ya za ki aikata wannan shiryen? Yanzu idan 'yan'uwa suka ji uban me kike so mu ce musu? Yanzu da aka ba ki gado wa za a kira ya yi jinyarki?" Na ce"To ai ba na shakkar kowa ya ji abin da ya faru, tun da dai na rabu da tsinken nan shikenan, idan ma zancen ya fito kai ne da kunya, kai ne za a zaga a ce ka cutar da ni". "Ya isa haka!" Ya daka min tsawa, sannan ya dora da faɗin"Duk wannan shirmen da kike yi ba zai hana ni bin umarnin mahaifiyata na yi aure ba, ko ki mutu ko ki rayu zan yi aure, don haka kina da zaɓi, ko ki kwantar da hankalinki ki cigaba da bin uamarnina mu zauna lafiya, ko kuma ki tada hankalinki ki yi ta shiga ƙunci da damuwa, kina kallo kuma ni zan samu kwanciyar hankali da matata". Ina kuka na ce"Ba zan yi maka biyayya ba, ba zan sake bin umarninka ba, kuma ba zan sake kwana a gidanka ba matuƙar ka auri wata, sai dai ka sake ni wallahi, ai ba kai kaɗai ba ne namiji". Wannan karon dariyar rainin hankali ya yi ya ce"Ba ni kaɗai ba ne namiji, amma ni kaɗai ne namijin da za ki rayu da shi har abada, ke da zaman aure da wani sai a lahira idan ana yi, kuma aurena da ke ki saka a ranki takalmin kaza ne, mutuwa ce kaɗai za ta rabu, don haka nan gaba idan kin tashi azabtar da kanki a wuyanki za ki saka wuƙar ba hannu ba, shashasha!". Ya tashi yana harara ta ya ce"Kar ki sake ki kira wani ki ce za ki yi kuskuren sanar da shi, zan nemo wacce za ta kula da ke, saboda ba zan iya kwana a asibiti ba". Na ce"Ba na buƙatar taimakon kowa, kuma ka kawo min wayata!". Ya fita ba tare da ya sake ce mini komai ba. Gida ya koma ya yi wanka, yana fitowa ya shirya ya nemi waje ya zauna ya riƙe kansa, bai taɓa tunanin ƙarfin zuciyar Sayyada ya kai ta aikata haka ba, ana wannan halin kiran Safna ya sake shigowa wayarsa, ya ɗauka a sanyaye yana faɗin"Baby". Ta ce"Beb lafiya ba ka ƙaraso ba?" Ya ce"Sorry ba zan samu zuwa, a halin yanzu ba na cikin nutsuwata ma wallahi". Ta ce"Subhanallah! Mene ne ya faru?" Ya yi guntun tsaki ya ce"Wannan mahaukaciyar yarinyar ce ta yanka jikinta". Gabanta ya faɗi ta ce"Ban gane ba, yankewa ta yi ba ta sani ba?" Ya ce"Ba na faɗa miki ta takura min sai ta haihu ba?" Ta ce"E ka sha faɗa min". Ya ce"To shi ne da na hana ta fita yau ta ɗauki wuƙa ta yanka hannun za ta cire". Safna a ranta ta ce'Matsiyaciya dama ta mutu, na huta' A fili kuwa sai ta nuna alamar damuwa, ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Amma dai yankan bai shiga sosai ba ko? Yanzu tana ina, na zo na duba ta?" Ya ce"Ki kwantar da hankalinki ai ba abar tausayi ba ce, a kanta aka fara kishi?" Ta ce"A'a bai kamata fa ka ce haka ba, ka san kowace mace da kalar nata tunanin wajen kishi, ka yi mata uzuri, ni wallahi tausayi take ba ni ma, yanzu kuna asibiti?" Ya ce"Na dawo gida, ba ta isa ta saka ni kwanan asibiti saboda haukanta ba, tunanin wacce zan nema ta kwana da ita nake". Da sauri ta ce"I can! Ba sai ka nemo kowa ba ni zan zo na kwana da ita". Ya ce"A'a Safna, kar ki takura kanki, kuma kin san idan ta gane ke ce ba za ta ji daɗi ba". Ta marairaice ta ce"Na yi maka alƙawarin ba za ta gane ba, wallahi ba zan nuna mata komai ba, ko dai ba ka yarda da ni ba ne Beb?" Ya sauke numfashi ya ce"Wallahi na yarda da ke, kawai dai na yi mamaki, na yi zaton kishi ba zai bari ki je ba". Ta ce"Wallahi tamkar yadda zan zauna da ƙanwata uwa ɗaya uba ɗaya haka zan zauna da Anti Sayyada". Ya ce"Na gode sosai my wife to be, amma a gida za a bar ki?" Ta ce"Duk da dai yau ba dutyn dare gare ni ba, amma zan ce zan karɓawa ƙawata saboda ɗanta ba shi da lafiya, za a iya barina". Ya ce"Wow! To bari na zo na ɗauke ki ko?" Ta ce"A'a, kar ka zo za a zargi wani abun, bari na zo kawai gidan sai ka kai ni". Ya ce"Za ki taho min da abincina da kika yi min? Yunwa nake ji". Ta ɗan yi shiru na sakanni kafin ta ce"A'a ba zai yiwu na taho maka da shi ba, za a zargi wani abun, ka ga an san kai na yi wa girkin, kuma yau ba ni da aikin dare, idan na yi ƙaryar zan karɓawa wata an yarda, ba za a yarda da ni ba idan na ɗauki abincinka". Ya ce"Good! Kina da tunani". Ta ce"Amma dai idan na zo zan dafa maka". Ya ce"Na gode sosai ina jiranki a bakin titi". Suka ajiye waya, yana sauke ajiyar zuciya. Sannan ya tashi ya fita da mota, bayan ya ɗakko ta a hanya tana ta nuna jimaminta, kamar ta fi shi son Sayyada, da suka ƙarasa gidan ita ta gyara wajen da jinin ya ɓata, sannan ta shiga kitchen ta ɗora masa macaroni jollof, a falo ya zauna yana ta danne zuciyarsa, da kuma shaiɗan ɗin da yake ta ƙissima masa ya gwada sa'arsa a kan Safna, ta taimake shi ko da romance ne, lokaci ɗaya fitinanniyar sha'awa ta taso masa, duk da Safna ko hijjabi ba ta cire ba. [21/09, 5:00 pm] Sadiya Abdulrazak: *KU YI MANA ADALCI* NA Sadiya Abdulrazak Page 3 3 Allah Ya sa aurenta yake son yi, duk da mutum ba ya hana kan shi jin sha'awar wanda ya yi masa, amma a yanzu dai ba irin yanayin baya yake ji ba, ji yake kamar ya gwada ta ko za ta amince ko sumbatarta ne ya yi, wata zuciyar tana hana shi, tunawa da yadda daren farkonsu da Sayyada ya kasance, ya ci wa daren buri sosai, amma ƙarshe sai ga shi ya zo masa a baibai, a ranar ko sha'awarta bai ji ba, haka suka kwana ƙalau ba wani abu da ya shiga tsakaninsu, haka aka kasance babu wani marmari da shauƙin juna, to gaskiya yana son yin ƙara'i a wannan sabon auren da zai yi, don haka ya daure ya dinga yaƙi da shaiɗan har ya samu ya fi ƙarfin zuciyarsa bai nunawa Safna komai ba, a baki ta dinga ba shi abincin, kuma har vedio ta yi masa, dama ta yi wasu a kitchen, bayan ya gama ci ta ce ya ɗakkowa Sayyada wasu kayan ko za ta yi wanka, ya ɗakko suka tafi, da abincin da kuma ruwan zafi. A hanya yake cewa"Allah Ya sa dai kar ta gane, don Allah ki yi iya yinki don ganin kin kaucewa yadda za ta sanki, tukuna ma me za mu ce mata? Ke wace ce?" Ta ce"Sai mu ce ni 'yar'uwarka ce, na zo zan kwana biyu, kuma za ka iya sirri da ni shi ne ka ce wa Momy na zo gidanka na kwana biyu kafin na tafi". Ya ce"Kai na gode Allah, da ya ba ni mace mai basira, i love You". Ta yi murmushi ta ce"Ai ka cancanci hakan ne Love". Lokacin da suka ƙarasa ɗakin bacci take yi, suka tsaya suna kallonta tana ta bacci, ya taɓe baki ya ce"Kin dai ganta, ga shirmen da ta yi abin da ya ja mata". Safna ta ce"Allah sarki, Allah Ya ba ta lafiya, kai ma kuma bai kamata ka kafe a kan ba za ta cire tsinken ba, yanzu ga shi ta cutar da kanta". Ya ce"Share ta". Ya fita ya siyo kayan shayi, biredi, kaza da fruit, ya kawo ya ce idan ta tashi sai ta saka ta ci abincin, suka zauna suna ta fira, yana tambayarta anya za ta iya kwana kuwa, dariya kawai ta yi ta ce ni da na saba kwanan asibiti, babu komai ka je kawai". Ya ce"To na gode sosai Baby, ku kwana lafiya". Ya fita yana waiwayenta yana murmushi, a ransa kuwa daɗi yake ji sosai, don ya fara hango yadda gidansa zai wanzu da zaman lafiya idan ya aure ta. Bayan fitarsa ta bi Sayyada da kallon wulaƙanci, wayarta da ya ba ta ta ajiye mata ta ɗakko, a hakanli ta ɗago yatsan Sayyadar ta ɗora a wayar key ɗin ya fita, ta sauke ajiyar zuciya ta matsa gefe, lambarta ta fara ɗauka, sannan ta shiga cikin wayar ta fara bincike, ba ta ga komai na rashin gaskiya ba, don haka ta ajiye mata, sai ta dubo lambar tata a whatsApp ta tura mata vedion Sadam wanda take ba shi abinci a baki, da kuma wanda take yin girki a kitchen, ta tura mata shi amma ta once, yadda idan ta kalla sau ɗaya shikenan ba za ta sake kalla ba, ta haɗa da rubutu a ƙasan ta ce"Ya kamata ki gane miji irin naki ba wanda za ki nasaka kanki a kansa ba ne, kin dai gani kina asibiti shi kuma yana tare da wata, cewa ya yi ya ji daɗin baki gado da aka yi ma, sannan ba zai iya kwana da ke ba, yanzu haka yana can tare da wata, ta yi masa girki kuma za ta kwana a gadonsa, ban faɗa miki don ki tada hankalinki ba, sai don ki nutsu ki gane da wa kike tare, mijin ƙaton mane min mata ne". Tana ta kallo a wayarta, don ta kunna data ba ta ga Sadam online ba, dama ya ce mata da wuri zai yi bacci, har ta gama ta yi bacci, Sayyada ba ta tashi ba, ita ma ta kwanta a sallaya ta lulluɓa da hijjabinta, bayan ta zare layin da ta tura mata saƙon da shi daga cikin waya, ta fara baccinta hankali kwance. SAYYADA Sai ƙarfe ɗaya na dare na farka, na bi ɗakin da nake da kallo, zuciyata ta fara zafi, ƙwalla ta zubo min, tunawa da duk ni na ja wa kaina kasancewata a nan ɗin, na kalli hannu na da ke naɗe da bandeji, yana yi min zafi har yanzu, hawaye ya sakko min, cikin wayam yunwa nake ji, fitsarin da nake ji da kuma tunanin ban yi sallar magriba ba da isha'i ba, ya sa na yunƙura na tashi zaune, gabana ya faɗi ganin wata kwance a ƙasan gadon, tsoro kuma ya ɗan kama ni, duk da na yi tunanin Sadam ne ya aiko ta, to amma wace ce? Na san dai ƙanwarsa Amna ko mutuwa zan yi ba za ta zo ta zauna da ni ba, saboda tsanar da ta yi min, kuma ban da ita ba shi da wata ƙanwa, sannan ba zai iya zuwa ya faɗa a gidanmu ba ballantana na ce ko Khadija aka ba shi, wannan ma babba ce ta fi Khadija ƙanwata, da wannan saƙe-saƙen na yi hanyar banɗaki, sai kuma idona ta sauka a kan wayata, na ɗauka na buɗe ta, da text massage na fara cin karo, wanda ke ɗauke da cewar "Ki duba na ajiye miki saƙo a whatsApp mai muhimmanci". Da sauri na kunna data na shiga whatsApp ɗin, hannuna har rawa yake yi, saƙon da na gani da baƙuwar lambar na fara buɗewa, na danna vedios ɗin, wanda take ba shi abinci a ba ki na fara gani, ina karanta maganar kuma hankalina ya ƙara tashi, wallahi saura kaɗan fitsarin da nake ya kufce min, da sauri na ƙarasa banɗakin riƙe da wayar ina jin kamar na saka kuka, kafin na yi alwala sai da na karasa kallon sauran, tabbas na gane kitchen dina, ga kuma falona, kuma shikenan ba ni da damar sake kallon vedion ballantana na kafa shaida da shi, zargina ya zama gaskiya, yau dai ta tabbata mijina yana neman mata, kamar yana jira na bar gidan? Na fashe da kuka sosai, ina alwala ina kukan, sai da na fito daga banɗakin na share hawayen, na ajiye wayar a gadon na shiga tashin wacce take baccin. "Baiwar Allah" Na faɗa ina taɓa ƙafarta, ta farka ta yaye fuskarta daga lulluɓar, gabana ya faɗi ganin ban santa ba, ban taɓa ganinta ba, za ta girmi tun a kallo ɗaya. Safna ta ce"Anti Sayyada sannu, kin tashi ashe". Na ce"Yawwa, amma wace ce ke?" Ta ce"Ƙanwar Yaya Sadam ce, zuwa ya yi gidan ya ɗakko ni zan kula da ke". Na ce"Na gode, ara min hijjabin zan yi sallah". Ta ɗakko jaka tana cewa "Ai ya haɗo miki ma da hijjabi a cikin kayanki". Na karɓa na saka, ta tashi ta ba ni sallayar na tada sallah, kafin na idar ta haɗa mini shayi, ta zuba min macaroni da kazar, zuciyata zafi take yi min, shi yasa na ɗaga hannu na daɗe ina ta addu'a Allah Ya sassauta mini abin da nake ji, har sai da na ji mai ciwon ya dame ni da zafi, sannan na sauke, ta kalle ni ta ce"Sannu Anti Sayyada ga abinci". Yunwa nake ji don haka na yunƙura zan ɗauka, amma da na tuna wai wata ce ta dafa abincin sai na koma na zauna, ƙwalla ta kawo idona na ce"Ya sunanki ke ɗin? Kuma ban san ki a 'yan'uwan shi ba". Ta yi murmushi ta ce"Sunana Hafsa, kuma ni da babar shi da babata uwa ɗaya uba ɗaya suke, ina yawan zuwa gidan ai, don dai ba kya zuwa ne sosai, su ma kuma 'yan gidan ban ga suna zuwa gidan naku ba shiyasa ba za ki san ni ba". Na ce"Ok, amma wannan abincin daga ina aka same shi?" Ta ce"E to, ni dai ya kawo ne kawai". Na ji sam ba zan iya ci ba, ba zan iya cin abin da karuwarsa ta dafa ba, duk da yunwar da nake ji haka na ƙi ci, na sha iya shayin, na ci ayaba, ta ba ni magani na sha na koma na kwanta ina jin zuciyata tana yi min nauyi. Sadam ya daɗe yana cutata, ya daɗe yana ƙuntata mini, tun kafin ya aure ni yake gana min azaba, sai yaushe ne zan fara morar garɗin soyayya wai? Bayan aurenmu na yi zaton shikenan ni da baƙinciki sai hange daga nesa, ashe zaman yana can a gaba, zuciyata dai ta dinga zuga ni a kan na bar asibitin nan kawai na tafi na je na rutsa shi da karuwar a yi wacce za a yi, ba tare da dogon tunani ba na tashi, na sauka daga gadon, na zura hijjabi, Safna ta kalle ni ta ce"Anti ina za ki je?" Na ce"Gida zan tafi, ni na ji sauƙi". Sai ta tashi da sauri ta ce"A'a don Allah ki yi haƙuri ki zauna har sai an sallame ki, kuma yanzu dare ya yi ma". Tsaki kawai na yi, na buɗe ƙofar na fita, da gudu ita ma ta fito ta shiga ofishin likitocin, ta sanar da su, sai ga likitan ya fito da saurinsa ya taddo ni ya ce"Madam ya haka, mene ne ya faru?" Na ce"Ka sallame ni kawai ni a gida zan kwana". Ya ce"Ki yi haƙuri ba zai yiwu na sallame ki yau ba, sai dai ko zuwa gobe, kin ga dare ya yi ai". Sai kawai na fara hawaye, sai yanzu ma na yi tunanin ba zan samu abun hawa ba ai, ya ce"Ki yi haƙuri ki koma pls". Safna ta kama hannuna tana ba ni haƙuri ita ma, ta ja ni sai na bi ta muka koma ɗakin, baccin da ban koma ba kenan, na ga tsayin daren sosai, na yi kuka na ƙoshi, na kuma tuna abubuwa da dama wanda a yanzu nake ndamar aikata su. Da asuba Safna tana yin sallah ta ce za ta tafi gida, za ta dawo min da abinci, na yi mata godiya, da ta fita tsayawa ta yi ta kira Sadam a waya ta faɗa masa ta bar asibitin, ya kamata shi ya je, ya ce"Na gode sosai Baby, amma fa ni ba zan fita yanzu ba gaskiya, sai zan tafi aiki sai na leƙa ta". Ta ce"Amma fa ya kamata ka je da wuri, don jiyan ma cewa ta yi ba za ta kwana a asibiti ba da ƙyar ta haƙura, likitan ya ce yau zai sallame ta". Ya ce"Au haka ma za ta yi? Ai da ya bar ta ta dawo ɗin, ta zauna idan hannun ya riɓe aka yanke kin ga ni ba zan zauna da musaka ba ai". Safna ta yi dariya ta ce"Ba ma zai faru ba, ka je dai don Allah, sai ka kai mata abincin kari, jiya shayi kawai ta sha". Ya ce"Gaskiya ni za ta takura ni, bacci bai ishe ni ba, ina ta tunanin ya kika kwana". Ta ce"Ya na kwana ko dai ya matarka ta kwana?" Ya ce"Wallahi ke nake tunani, an ɗora miki nauyin da ba naki ba, ga shi ina fargabar kar ta gano wace ce ke a samu matsala". Ta yi dariya ta ce"Idan ma aka gane ba na jin za a samu matsala ai na ga Antin tawa tana da haƙuri". Ya ce"Za ki jira na zo na ɗauke ki?" Ta ce"A'a zan tafi a adaidaitasahu, zan yo muku girkin kai da ita sai na dawo". Ya ce"Me zai hana ki zo ki yi a nan gidan namu? Please". Ta ce"To bari na zo ɗin". Ta ɗan jima a tsaye kafin ta samu adaidaitasahu ta hau, ta kama hanyar gidan Sadam, da ta ƙarasa kiransa ta yi ya zo ya buɗe mata, suka ƙara gaisawa, ta shiga kitchen da sauri, ya bi bayanta yana jin yadda yanayinsa yake canzawa, sai dai yana ta ƙoƙarin dannewa, kayan ciki ta gyara ta ɗora sannan ta ɗora shayi, ta ɗakko doya tana firewa, shi kuma yana ta kallonta fa burgewa, ji yake ina ma a ce an yi auren matarsa ce, da babu abin da zai hana shi rungume ta ko zai ji sassaucin yadda sha'awarta take gigita shi, amma babu dama, a gaskiya bai taɓa gwada yi mata ko maganar batsa ba, bai sani ba ko za ta amince da romance, ya dinga sauke numfarfashi, yana amsa mata firar da take yi masa da e, ac, har dai ta ce"Beb ko ba ka da lafiya ne?" Ya ce"Lafiya ba lau ba". Ta ce"Mene ne yake damunka?" Ya ce"Ke ce, kewarki ce za ta kassara ni". Ta ce"Kewa kuma? Ba gamu a tare ba?" Ya ce"Ba irin wannan kasancewar ba ai, zan so wacce ta fi wannan kusanci". Ta yi murmushi ta ce"Ni dai ban gane ba, kuma ba na so na na gane, pls mu bar zancen". "Ok" Kawai ya ce, ya tashi ya bar kitchen ɗin, ta bi shi da kallon tausayi cikin shauƙin so da ƙauna. Har ta kammala komai bai dawo kitchen ɗin ba, ta zuba wanda za a kai wa Sayyada, ta zuba masa na shi ta fito falon, ta same shi kwance a kujera, ta ajiye tana cewa"Na yi zaton ma ka yi wanka kana karyawa sai dai kawai ka tafi kai mata?" Ya sauke numfashi ya ce"Yanzu zan yi, za ki taya ni ko?" Ta yi kamar ba ta ji shi ba, ta ce"Ka ci abincin". Ya ce"Ki zo mu ci mana". Ta girgiza kai alamar a'a. Ya ce"Don Allah zauna mu ci, ya min yawa ma ai". Ta zauna suna ci suna kallon soyayya da murmushi, har wanke-wanke ta yi ta gyara komai tsaf, ta juyo za ta bar kitchen ɗin, ta gan shi tsaye ya tare hanya, kuma ba kamar ɗazu ba da yake da jallabiya a jikinsa, yanzu gajeren wando ne kawai a jikinsa, da alamar kuma daga wanka ya fito, tsoro ya kama ta, kafin ta yi magana ya ce"Safna can I give you a huge? Please my wife to be". SAYYADA Na yi zaton tun asuba Sadam zai zo, na ji shiru har gari ya waye, ga yunwa ina ji, ina cikin jerin mutanen da ɓacin rai ko jinya ba ya hana su cin abinci, ko macaroni da ban ci ba jiya kishi ne, na ƙara haɗa shayi na sha, na ci kazar, don da na duba ta na fahimci gashin bakin titi ne ba ita ce ta gasa ba, ina ci ina hawaye, idan na tuna Sadam yau ya kwana da wata a gadonmu na sunna sai na ji kamar rayuwata ta zo ƙarshe, fitar numfashina har canzawa ya yi. Wajen ƙarfe tara da rabi na gaji da jiran shi, na daure zuciyata na ɗauki waya ba kira shi, kira biyar bai ɗauka ba, zuciya tana ta raya min yana can tare da mace sun ɗora daga inda tsaya daren jiya, sai na ji ba zan iya cigaba da zaman asibitin ba, duk da da safen nan da likitan ya duba ni ya sake ba ni haƙuri ya ce na bari Sadam ɗin ya zo sai a ji yadda za a yi, sai ya dinga zuwa gida yana duba ni kullum, amma na kasa haƙuri na tashi na ɗauki wayata na saka hijjabi na fice, Allah Ya taimake ni har na bar cikin asibitin ba wanda ya gane ba ni da gaskiya. Na tari adaidaitasahu na hau, a hanya ma sai hawaye nake yi, ina kuma fargabar abin da zan je na tarar, wallahi Indai ya tabbata da wata a gidan dole ya sake ni duk taurin kansa. 08028966015 [24/09, 9:26 am] Sadiya Abdulrazak: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LnQJ26F7GLvLHNQHkwpWw1 *KU YI MANA ADALCI* NA Sadiya Abdulrazak Page 4 Assalamu Alaikum my people dafatan kunanan cikin aminci sunana ummuh sayyeed traditional medicine center Zaria dealer in all kinds of magungunan mata turarukan wuta sudaniss dilka skin care products Alhmdulillah call 09065504546 Ina mai farin cikin sanar da Yan uwana mata ni yar mutan Chadian zan muku promo 🎤🎤🎤🎤 Tundaga gobe__ 9/19/2025__ harzuwa end of this month dinnan in Sha allahu Ina matanda sukefama da rama Ina masu fama da lalacewar nono Ina matanda sukefama da rashin gashi da lalacewar gashi Ina Maison taga komai nata cifcif Ina Mai Hmmm kukanki yazo karshe dakila wadda ita batasan Dadin jima'ba shin kinsan ko mijinki ne bai baki abinda kikeso wato baida kuzari munada maganin da zamubashi Ga kayan dazamu yi promo Nan akan 4,500 kacal 👌👌 Maganin sanyi 1,k Tsumin bom 1,500 Madarar tabaje 1k Gumbar Milo 1k Garin yaukayauka emergency 1,500 Garin kinfi kaza 1,500 Hmmm duk waddanan kayanfa ,naira 4,500 💃 munamaraba damasu siyan Daya ko sari Page 4 Muna dab da ƙarasawa gidan na hangi wata mace ta fito daga gidan tare da Sadam, ƙirjina ya doka da ƙarfi, sai dai kafin adaidaitasahun mu ya ƙarasa tuni ta hau adaidaitasahun da ya zo wucewa an ja sun tafi. "Tsaya! Sauke ni haka!" Na faɗa da ƙarfi don ganin Sadam ya juya da sauri zai koma cikin gidan, ko gama tsayawa bai yi ba na fito hakan ya sa na faɗi a ƙasa tim, ban damu ba na miƙe da sauri na cim ma Sadam da yake shirin shiga gidan, shi kuwa wata kunya ce da fargaba ta kama shi, saboda ya san dole ta fa Safna, kuma sai yake ji kamar za ta gane ya rungume Safna har ma ya yi kissing ɗinta a cikin gidansu. Da sauri na fizgo jallabiyar jikinsa cikin ƙaraji na ce"Wace ce wannan!? Sadam da wa ka kwana a cikin gidana?" Yana juyowa ya sharara mini mari, rai a haɗe ya ce"Ashe ba ki da hankali! Ni za ki yi ƙazafi a titi a bainan nasi?" Na ci kwalarsa na fashe da kuka ina cewa"Ni za ka mara a kan hakkina? Ba zan sake yarda ka ci zarafina a kan gaskiya ta ba wallahi, wace ce wannan ka rako ta? Uban me ya kawo ta gidana da sassafe? Kuma uwar wace ta yi maka girki juya a cikin gidan nan?" Da ƙarfe ya ƙara min marin, sannan ya fizge rigarsa, takaici da zafin zuciya suka saka ni zubewa a wajen na rushe da kuka, ga shi ƙofar gidanmu titi ne, masu ababen hawa har sun fara fakawa suna kallonmu, cak ya ɗauke ni ya yi cikin gidan da ni, ina ta zillewa ina zagin shi ina faɗin"Ka ajiye ni, wallahi yau sai ka sake ni, kuma ba zan taɓa yafe maka ba, ɗan iska, fasiƙi, mazinaci". "Kar fa ki fama hannunki, ba ki da hankali ne?" Ya faɗa kamar bai damu da zagin da nake yi masa ba. Bai ajiye ni ba sai da ya sada ni da ɗakina, ya kulle ƙofar, duk da ba a hayyacina nake ba, amma idona tarr ya sauka a kan gadona, inda na ga pant yashe a gadon, an buɗe shi kamar wanda aka shanya shi, tashin hankali bai sa na tsaya na yi wa wandon kallon tsanaki ba, da tabbas zan gane nawa ne, na zauna a jikin ƙofar na ɗora hannu a kai na rushe da kuka ina cewa"Na shiga uku, Sadam ka cuce ni ba zan taɓa yafe maka ba". Duk wannan ihun da nake yi yana falo yana jiyo ni, shi ma kuma abun duniya ya ishe shi, ya yi nadamar gayyato Safna, Allah ne shaidarsa bai taɓa kusantar wata mace ba bayan Sayyada, duk 'yan tsalle-tsallensa a iya waya yake ƙarewa, wannan ta san yana yi, yana yin sex chart har ya samawa kansa nutsuwa, amma ya sani a yadda soyayyarsa da Sayyada ta kasance kafin aure dole za ta iya zarginsa a yanzu, ai shi ne ya zubar da garinsa a wajenta, amma idan za ta yi masa adalci tun da bai zarge ta ba, bai kamata ita ma ta zarge shi ba, dalili kuwa shi ne ita da shi ɗin ƙwaryar sama ce ta daki ta ƙasa. "Sayyada aurenki fa zan yi, an saka ranar aurenmu, ɗaurawa ne kawai ya rage, idan ba ki yarda da ni ba a yanzu sai yaushe? Ashe ba ni da wata alfarma a wajenki? Ba ni da matsayin da zan nemi abu ki ba ni? Please just romance, ki amince da ni, ba za ki taɓa danasani ba". Na rintse ido tunawa da irin kalaman yaudarar da ya dinga yi mini, nuna mini yake duk matan duniya ma shi ƙyamar su yake, da ni kaɗai zai iya sex, ashe zai iya maimaitawa wata macen wannan kalaman da ya yi mini amfani da su har na amince? Kuma idan ta amince har ya aikata? Lallai duk wacce ta yarda da daɗin bakin namiji za ta sha giyar mamaki ta yi mankas har ta yi tuɓumle, ni Sayyada kura-kuran da na yi a kan Saddam sai dai na roƙi Allah Ya yafe mini kawai, amma na tabbata shugabar daƙiƙan matan duniya, a gaba za ku ji labarin kalar tawa soyayyar. Na ci kuka na gode Allah, a nan ƙasan ɗakin bacci ya kwashe ni ban shirya ba. Sai da ya daina jin kukana sannan ya buɗe ni, a zatonsa na yi haƙuri ne, sai ya same ni ina bacci, ɗaukata da ya yi don mayar da ni kan gado ne ya farkar da ni, na sauke idona a cikin nashi, na zabura zan dire sai na fama ciwona, na saki kukan azaba ina jin dama kawai na mutu na huta, don ganin Sadam yana azabtar da ni ba kaɗan ba. "Sorry Sweetheart". Ya kira ni da sunan da yake yi min daɗi a da, amma yanzu haushi na ji maimakon daɗin. "Ka ajiye ni". Na faɗa ina hawaye Ya ce"Ok" Ya ɗora ni a gadon. Na ce"Na tsane ka!". Ya ce"Ki dakata da wannan shirmen please, ya jikin naki?" Na haɗiyi yawun baƙin ciki, ban da raini ni zai tambaya ta jiki? Na rufe ido kawai hawaye yana sake kwaranya daga idona. Ya ce"Ki tashi ki ci abinci ki yi wanka ko za ki daɗin jikinki". Na yi shiru ban kuma buɗe idona ba, tabbas Allah Ya taimaki Sadam da ya ƙaddara wannan ciwon na hannuna, da yau ban san adadin haukan da zan nuna masa a cikin gidan nan ba, ganin na lumshe ido ya yi zaton bacci nake yi, sai ya tashi ya bar ɗakin, yana fita na tashi leƙa shi ta window, na hangen shi a falo yana waya, ba dai na jiyo abin da yake cewa, yana shiga ɗakinsa na saka hijjabi da takalmi da sauri ko wayata ban tsaya ɗauka ba, na fito cikin sanɗa na bar falon, Allah Ya taimake ni mai gadi yana cikin ɗakinsa, don haka na buɗe gidan na fita, Allah Ya sake taimakona na fita daidai adaidaitasahu ta ajiye maƙocinmu, na faɗa ina faɗa masa ya yi sauri ya ja mu tafi, ai kuwa ya bi umarnina ya fafake mu a guje yana tambayar lafiya? Na ce"Mahaukaci ne ta biyo ni, kuma gudu gare shi kamar babur". Ya ce"Subhanallah! Gaskiya to ba ki kyauta mini ba, salon ya yi jifa ya fasa kin glass?" Ya ƙara gudu sosai, cikin sakanni muka bar unguwar. Na yi iya ƙoƙarina na ganin na saita kaina kafin na shiga cikin gidanmu, na shiga ɗaki na gaishe da Mama na ce ta ba ni ɗari biyu zan bawa mai adaidaitasahun, ta ba ni, na fita na kai masa, sannan na dawo ɗakin, na zauna na sunkuyar da kai. Ta kalle ni ta ce"Sayyada lafiya kuwa? Na gan ki a hargitse me ya faru?" Sai na fara kuka na ce"Babu komai". Ta ce"Babu komai za ki zo haka ba shiri ki saka ni a gaba da kuka? Ba za ki faɗa ba? Ko ke da Sadam ɗin ne?" Na gyaɗa mata kai alamar e, don na shirya sanar da ita abin da yake faruwa, saboda a yadda nake ji a raina kawai na gama zama da Sadam, damuwa ta bayyana a fuskarta ta ce"Mene ne ya faru? Wani abun ya yi miki?" Daidai nan kuma Baba ya yi sallama a ɗakin, na gaishe shi, bai amsa ba ya ce"Sayyada, kukan ne kike yi?". Mama ta ce"Ita da mijinta ne, yanzu nake son jin mene ne ya haɗa su". Nan take Baba ya haɗe rai kamar hadari, ya ce"Ba na son jin komai da ya shafi zaman auren Sayyada da yaron nan, don haka tashi maza ki koma ɗakinki". Mama ta ce"Amma Malam ba ta taɓa kawo ƙararsa ba, ya kamata a tsaya a saurare ta a ji da me ta zo". Ya ce"Ko da me ta zo ba mu da maganinsa, na dai shi ta zaɓa ba? To ta je ta rayu da shi, ko kashe ta ya yi sai dai na ce Allah Ya ji ƙanta, ba dai na ɗaga kai na yi masa kallon banza ba". Na fashe da kuka na ce"Baba don Allah ka yi haƙuri ka yafe min, wallahi na gaji da auren nan, kuma na yi nadama". Ya ce"Nadamarki ta zo a makare, kar ma ki sake ki furta abin da ya yi miki, ni sai dai ma na ce ya yi min daidai, kuma daga yau kar na sake jin wata matsala ta kawo ki gidan nan, tun daga ranar da na ba shi ke na faɗa muku kyauta ce ta har abada idan ya ga dama ya kwaɗa ki ya cinye, ko sakinki ya yi dama kar ki tunkaro gidana, tashi ki koma!" Ya karasa da daka min tsawa. Na kalli Mama sai na ga ta kau da kai daga kallona, haka na fita ina gursheƙen kuka, ina tafe a hanya ina kuka kamar mara galihu ko wata ƙaramar yarinya, ba na ma kallon gabana kawai jefa ƙafata nake yi, a raina ina tambayar shin wace irin zuciya ce da babana? Allah mamallakin kowa da komai ma muna yi masa laifi ya yafe mana, shi Baba me yasa ba zai yafe min ba? Horn ɗin mota na dinga ji babu ƙaƙautawa ta bayana, don haka na waiwaya don na ga ta ina na tarewa mai motar hanya, sai na ga motar Sadam ce, na juya na cigaba da tafiya, ya fito daga motar da sauri ya sha gabana ya ce"Ki zo ki shige mu tafi, ai dama kin san ba ki da wani sauran matsuguni a gidanku, ina fata dai haukanki bai yi tsananin da har kika faɗa musu abin da ya faru ba". Ina kuka na ce"Abin da ya faru wanne daga ciki? To wanda kake gudun shi na faɗa musu, na faɗa musu kai mazinaci ne, fasiƙi". Ya ɗage kafaɗa ya ce"Fine! Ai dama sun san ni da ke mazinata ne tun tuni, don ba a mazinaci sai da mazinaciya". Na ji maganar kamar saukar aradu a kaina, kafin na nemi amsar ba shi, ya fizgi hannuna mai lafiyar ya ja ni zuwa wajen mota, ya buɗe ta ya tura ni, idan ma bai tura ni ba shigar zan yi wallahi, don yanzu na fahimci da gaske gidan nashi da nake ganin shi ne damuwata zaman cikinsa ya zame mini dole, sai ranar da baƙinciki ya yi ajalina zan bar shi, ya shiga motar ya ja muka tafi, na kifa kaina a cinyata ina ta rera kuka, bai yi min magana ba har muka ƙarasa gidan. 08028966015 [24/09, 5:27 pm] Sadiya Abdulrazak: Shi ya buɗe min motar na fito, ya kama hannuna kamar gaske muka shiga falon, ya zaunar da ni a kujera, shi ma ya zauna yana riƙe da hannuna ya ce"Sayyada, Allah Ya sa dai ba ki faɗi abin da kike zargi a gidanku ba, wallahi dariya ma za a yi miki". Na ce"Au zargi ma nake yi kenan? Har yanzu kana da ƙwarin gwiwar da za ka kare kanka duk da shaidun da na gani da idona? Sadam wace ce ta zo ta kwana a gidan nan? Idan za ka yi zinarka ba za ka yi a waje ba sai ka ci mutuncina ka zo har cikin gida a gadona?" Nan take yanayin fuskarsa ya juye daga na damuwa zuwa ɓacin rai, ya ce"Ke Sayyada kar ki sake danganta ni da zina, idan kuma zargina kike yi to ki fara saka minjaye, e ina nufin ni ma ina zarginki". Gabana ya faɗi na kalle shi hawaye yana sakko min na ce"Me na yi na zargi? Sai ka faɗi hujjarka". Sai ya yi tsaki ya ce"Kin ga ni ba na son tashin hankali, mu bar zancen haka, tabbas na kawo wata ta yi girki, amma wallahi babu abin da ya shiga tsakanina da ita, ni ba mazinaci ba ne Sayyada, wallahi ke kaɗai na sani a 'ya mace". Na girgiza kai na ce"Faɗi wata maganar dai, don har abada ba za ka samo kalaman da za su wanke ka ba, tun da ba zargi nake yi ba na tabbatar". Ya ce"Kin tabbatar? Shaidar zina ba fa ba ƙarama ba ce Sayyada, kin taɓa kama ni turmi da taɓarya? Kuma kin kira shaidu sun shaida? To wallahi ki iya bakinki, ki kiyaye ni". Na tashi zan tafi ya janyo ni na dawo, sai na zauna ɗin na kifa kaina a kujera, ba kuka nake ba, kawai dai na rasa ma yadda zan yi, shiru na sakanni kafin ya sanyaya murya ya ce"Sayyada". Ban amsa, ya fara faɗin"Duk iya ƙoƙarin da zan yi don na ga mun zauna lafiya ba tare da shiga hakkinki ba ina yi, ina ta gudun cutar da ke amma ke kamar ba kya gani, idan kina wani abun sai na ga kamar kin manta wane ne ni a wajenki, kamar kin manta ramukan da kika tsallake kafin burinki ya cika ki same ni, a zatona ko ni ne na sake ki don raɗin kaina ba za ki iya cigaba da rayuwa ba, amma yau wai ke ce kike cewa na sake ki, to ba zan sake ki, don haka ki kalle Ni mu tattaunawa kowa ya gyara halinsa, ina so zamanmu ya dawo kamar na baya, ba na jin daɗin ganinki a damuwa". Na yi shiru ina ta hawaye, ya ɗago ni yana cewa"Ki yi magana don Allah, kin ji?" Na ce"Sadam, za ka iya fasa wannan auren da kake shirin yi?" Ya ce"Wallahi ba zan iya fasawa, ai na faɗa miki umarnin mahaifiyata ne, kuma ba na haɗa umarninta da na kowa a duniyar nan, ba zan iya bijire mata ba". Na ce"Duk da na san Momy ba sona take ba, amma a wannan karon ba don ta ƙuntata min ta sa ka aure ba, don ka samu haihuwa ne, kuma yanzu tun da an cire tsinken ai zan haihu, me zai hana ka ce mata ta ɗan ƙara maka lokaci? Idan na samu cikin sai ka ce mata kawai ka fasa, ai ba za ta ƙi ba, tun da haihuwar da take fata za a samu". Ya ce"Ita kuma ya zan yi na wanke ta daga ganin baƙinta da za a yi? Ina nufin su gidan su yarinyar da za a aura min ɗin, kin ga za su mayar da ita ƙaramar mace idan ta dawo ta ce an fasa, sannan auren nan saura watanni biyu, kina da tabbacin za ki samu a cikin wata biyun?" Na ce"Idan na samu a cikin wata biyun za ka san yadda za ka yi a fasa auren?" Ya ce"Ban yi alƙawari ba". Na ce"To tun da hakane babu amfanin na tsaya ina tattaunawa da kai, aure dai sai ka yi ko? Ka je ka yi, amma ka sani daga ranar da ka auri wata ba zan sake amsa sunan matarka ba". Sai ya yi dariya ya ce"Za ki saki kanki ne ko kuma kotu za ki je ta raba mu?" Na ce"Ko da ina nan da aurenka ba za ka sake haɗa jiki da ni ba, na bar mata kai har abada". Ya ce"To shikenan, hakan ma ya yi indai za ki samu nutsuwa". Na tashi zan shiga ɗaki ya ce"Anjima kaɗan likita zai zo ya duba ki". Na gyaɗa kai, still ya sake riƙo hannuna, ya ce"Don Allah ki daina zargina, ban kwana da wata mace ba, amma wacce zan aura ta zo ta yi girki, kuma ita ce kika ga fitarta daga gidan ɗazu, Allah ne shaidata, ke ma kuma ki yi min adalci, tun da tare kuka kwana a asibiti da ita, yanzu ma ta dawo ne don ta yi miki abun karyawa, don Allah ki sassautawa zuciyarki". Takaicinsa ya linku a zuciyata, inda ya san zafin da zan ji da ya gwammace ya ɓoye min gaskiya, don wallahi a yadda nake da kishi har gara a ce wata karuwa can ya ɗakko haya a titi ta zo suka kwana a gidan, da a ce wacce zai aura ce ta zo ta yi mini girki a kitchen har ma ta zo ta taya ni kwana a asibiti, to idan da na san ita ce sanda na farka tana baccin nan da ban shaƙe shegiya ba na wuce lahira? A tsayen da nake na rushe da kuka ina maimaita idan ka cuce ni Allah Ya saka min, Allah Ya bi mini hakkina". Ya yi tsaki ya shige ɗakinsa, ni ma nawa ɗakin na koma na zauna ina fashewa da sabon kuka. A hankali kuma na taƙaita kukan, kafin ma ya ɗauke cak kamar an yi ruwa an ɗauke, ƙwaƙwalwata ta shiga tariyo mini shuɗaɗɗun lokuta masu daɗi a wajena da akasinsu. A asibiti muka haɗu da shi, lokacin Mama ba ta da lafiya an ba ta gado, shi kuma ranar ya je duba jikin abokinsa, Allah Ya ƙaddara haɗuwarmu, da fari ya fara ne da kallona yana faɗin na yi masa kama da wata Zainab a Kaduna, na faɗa masa ni ba ni da wata 'yar'uwa mai suna haka a Kaduna, ya dage ya ce dole 'yar'uwa ta ce tun da kamarmu ta ɓaci, har dai Anisa ta shiga zancen ta ce to ya nuna mana hoton Zainab, ya ce ba shi da hoton amma na ba shi lambata idan ya sa ta turo masa zai tura min, wannan ne silar haɗuwarmu da kuma faruwar komai, hoton Zainab kuma har yau bai nuna mini ba, ƙarshe dai ma ya sanar da ni babu ita, kawai yana neman link ɗin da zai jona alaƙarmu ne. Kafin a sallami Mama ya yi zuwa biyu asibitin, bayan an sallame ta kuma ya zo gida ya sake duba ta, nan fa ya riƙe ni sosai a waya, muka saba, amma har lokacin bai yi zancen yana sona ba, sai dai fira kawai kala-kala, har ta kai duniya fira da shi ta fi yi min daɗi sama da kowa, shiyasa kuwa idan bai kira kira ni sai na ji kamar ba ni da laka duk na rasa kuzarina, iyayena duk a zaton su soyayya muke yi, kamar yadda ni ma na yi zato, domin kuwa zuwa lokacin na kamu da soyayyar shi da ƙarfi kuwa, a zatona tun da yana ta nuna mini alamomin soyayya ai ba sai ya furta ba, akwai ƙawata da take faɗa min ita ma daga gaisuwar mutunci da firar duniya, ba ta san lokacin da suka faɗa soyayya ba, kawai sun wayo gari ne sun tsinci kansu a matsayin masoya, tsakanin ita da shi babu wanda ya yi zama na musamman ya yi wa ɗan'uwan shi bayanin na ga ni ina so, za mu fara soyayya, ga shi yanzu har sun yi aure, shi yasa na yi zaton ni ma haka ce za ta kasance mana ni da Sadam, don haka na ƙara zura jiki, saboda ni idan ina yin soyayya ina yinta da duka zuciyata da ƙarfina, haka ma idan ina ƙin mutum, akwai Ashiru, wani ɗan'uwan Babana da yake sona tun ina yarinya, ni kuma na tsane shi, da fari ya dage ya ce zai iya zama da ni ko ba na son shi, amma da na matse lamba wajen nuna masa ƙiyayyata tsirara a hankali na fita daga ransa ya janye da kansa Mun riga mun saba da Sadam, kullum muna tare a waya, duk ranar Alhamis da Juma'a da ba mu da islamiyyar dare yake zuwa mu sha fira, ganin shi shi ne babban farincikina, shi yasa nake alla-alla ranakun zuwan nashi su zo, dangi kowa ya ji na samu wanda zan aura, ballantana kuma ƙawayena wanda yanzu ba ni da wata fira sai ta Sadam, mun yi wata shida tare da shi sannan na yi kammala secondary, kuma a bisa tsarin Baba dama 'yarsa mace tana yin Candy sai zancen aure, ko ɗar ba na ji, tun da na san ina da mijin da zan aura, sati na ɗaya da Candy Baba ya zaunar da ni da batun aure, ya tambaye ni akwai wanda nake so? Nan take na faɗa masa ina da Sadam. Wata ranar Alhamis da Sadam ya zo, kafin na fita Baba ya tsare ya ce masa ya ba shi sati ɗaya ya turo magabatansa idan da gaske yake, ya ce masa to. Da na fito sai na ga fuskar Sadam a murtuke ba kamar yadda ya saba ba, hankalina ya tashi, saboda ni fa farincikinsa shi ne nawa a lokacin, na ce"Yaya Sadam, me ta faru na ga kana ɓata rai?" Ya yi shiru kamar ba zai ce komai ba, kafin ya sauke numfashi ya kalle ni ya ce"Ke Sayyada!" Na yi mamakin jin yadda ya danganta sunana da ke, sannan ya kaurara murya. Na gama can jinin jikina ni na yi masa laifi, gabana sai faɗuwa yake yi, kamar zan yi kuka na ce"Na'am". Ya ce"Mene ne alaƙata da ke?" Wannan tambayar tasa sai ta saka ni a ruɗani da fargaba, na ce"Yaya Sadam, ai ka fi ni sanin amsar wannan tambayar da ka yi mini, akwai wata matsala ne? Duk na rasa gane kanka". Ya ce"Ina son jin amsar nan daga bakinki, saboda na lura yadda na ɗauke ki ba haka kika ɗauke ni ba, mene ne alaƙata da ke? Ina nufin mene ne ya haɗa mu, me muke yi?" Na sunkuyar da kai na ce"Mutunci ne ya haɗa mu, daga baya kuma muka jone muka zama ɗaya, ina nufin soyayya muke yi ko?" Ya ce"Tun da muke da ke na taɓa cewa ina sonki?" Na ji kamar an rufto min wani abu a kaina, na ji kawai na fi kowa shiga muzanci a duniya, ga shi ba ya ko murmushi ballantana na yi tunanin wasa yake yi min, nan take idona ya tara ruwa suna dab da fara tsiyaya, shi kuwa ko a jikinsa ya sake maimaita"Na ce ina sonki ne? Dama soyayya muke yi?" Na saki hawayen da rawar murya na ce"Dama ba ka sona Yaya Sadam, don Allah ba na son irin wannan wasan". Ya ce"Ba wasa nake yi miki ba Sayyada, ni fa kawai na ɗauki alaƙarmu ne a matsayin abota da kuma girmama juna, ki yi haƙuri gaskiya ban taɓa jin son ki ba ballantana na yi tunanin zan aure ki, don haka ki sanarwa iyayenki ba soyayya muke yi ba tun wuri". Daga haka ya shiga motarsa ya ja ya tafi ya bar ni tsaye kamar an shuka ni, na kasa ko motsi, zuciyata sai tiriri take yi, na ja ƙafa ina share hawayena na shiga gida, Allah ya taimake ni babu kowa a tsakar gidan, na faɗa ɗakinku na kwanta a katifa na fashe da kuka, ƙannaina suka shiga tambayata mene ne, na ce kaina ke ciwo, Mama ba ta yarda da ni ba, kuma tambayar duniya na ƙi faɗa mata, a wannan daren ban runtsa ba, ko da a ce zan iya haƙura da soyayyar Sadam to da wane kalaman zan sanarwa duniya silar rabuwarmu? Sai na ce dama ba sona yake ba ni ce nake haukana? Washegari na tashi jiki ba ƙwari, dayake ranar Asabar ce na tafi Islamiyya ta safe, idan muka dawo ƙarfe ɗaya shikenan ba a komawa sai kuma ta dare, a makarantar ma yau ban tsinci komai ma, kifa kaina a benci kawai na yi na ce ba ni da lafiya. Ƙaramar magana da ta zama babba, ta tabbata Sadam da gaske yake ba wasa yake yi mini ba, tun da ga shi bai sake kirana ba har dare ya yi, na kasa jurewa na kira shi, sai ya kashe ya kira ni kamar yadda ya saba, na ɗauka da rawar murya, shi kuma muryarsa ba kamar yadda ya saba ba, sam babu walwala ya ce"Sayyada ya aka yi?" Na ce"Don Allah idan wani laifin na yi maka ka sanar da ni". Ya ce"Laifi ai ke ce kika yi min, a kan me za ki faɗawa mahaifinki soyayya muke yi, har ya tare ni da zancen ya ba ni sati ɗaya na turo iyayena? Na ce ina sonki ne?" Na fara kuka, na kasa cewa komai, zuciyata kamar za ta buɗe ƙirjina ta fito. Ya sassauta murya ya ce"Sayyada". Da ƙyar na ce"Na'am". Ya ce"Sona kike?" Na ce"Ka yi haƙuri idan na yi katsalandan a cikin rayuwarka, ba laifina ba ne, laifin zuciyata ne, kuma ni a nawa tunanin duk wani namiji da zai nunawa mace irin kulawar da kake ba ni sonta yake yi, shi yasa ma ban kwaɓi zuciyata ba, ashe na yi kuskuren fahimta, ina sonka Yaya Sadam, ina tsoron halin da zan shiga idan da gaske ba ka so na, don Allah mene ne aibuna?" Ya sauke numfashi ya ce"Ba ki da wani aibu, kuma zan iya soyayya da ke wannan ba wani abu ba ne, sai dai ni gaskiya ina da sharuɗan da na tanadarwa duk wacce zan yi soyayya da ita kafin ma a kai ga auren, kina ganin za ki iya bi?" Aka ce wanda yake ruwa idan aka miƙa masa takobi kamawa yake yi, a yanzu neman mafita nake yi, don haka na ce"Na amince". Ya ce"To saboda muhimmancin maganar, mu bar wa gobe in sha Allah zan zo sai mu tattauna baki da baki". Na ce"Allah Ya kai mu, na gode". Ya ce"Ni ma na gode, ki yi bacci mai daɗi". Zan iya cewa tun daga wannan ranar da Sadam ya karɓi soyayya rayuwarmu ta canza, rikiɗa ya yi ya koma kamar wanda ban san shi ba, kamar ba wannan wanda muka yi sabo muka zama abokan juna ba, sai ya yi ta sha min ƙamshi yana zuba izza, ni kuwa kullum soyayyarsa ƙara faɗi take yi da tsayi a zuciyata. Dokokin da ya kafa mini su ne, duk wani umarni da ya ba ni ya zama dole na bi, aurena zai yi, don haka bin umarninsa a yanzu shi zai tabbatar masa da ya yi dacen mace, kuma bayan auren za ta iya bin umarninsa, akasin haka kuwa tana nuna ko an yi auren bai isa da ita ba, don haka babu batun ya auri wacce ba za ta yi masa biyayya ba, cikin biyayyar nan har da sharaɗin tambayar shi duk inda zan je, dole sai ya san shige da ficena, ko da kuwa iyayena ne suka aike ni, sannan yana da damar ya bar ni na fita, yana da damar hana ni idan ya ga fitar da zan yi ba ta dace ba, na ce na amince. Sannan ya ce ba zan sake saka gyale ba, babu ni babu kwalliya sai dai idan zai zo zance, duka na amince, ya ce idan ya gan ni da wani saurayi ko ana gobe ɗaurin aurenmu ne ya fasa, na ce na amince, a haka muka gina soyayyar kuka ta fara tafiya sannu a hankali, ina ta ƙoƙarin bin dokokin nashi, sai da ta kai har Mama za ta aike ni idan na faɗa masa ya ce ba zan je ba, kuma ba zan je ba ɗin, sai dai na yi ƙaryar ba ni da lafiya saboda na kaucewa aiken, daga karshe ko unguwa na je shi zai ba ni lokacin da zan dawo gida, idan aka samu matsala na wuce ba ƙaramin ɓaci raina yake yi ba, sai na ta bin kansa kafin na samu ya yafe min mu shirya, shi yasa nake taka-tsan-tsan da duk abin da zai sa na karya dokarsa. Tun a cikin satin da Baba ya yanka masa ya turo Iyayensa aka saka ranar aure watanni takwas, shiyasa yanzu duk dangi kowa ya tabbatar da shi zan aura. 08028966015 [25/09, 4:11 pm] Sadiya Abdulrazak: Tun ina ɓoyewa makusanta yadda Sadam yake juya ni, ni kuma nake bin umarninsa kamar shi haife ni, har abun ya bayyana kowa ya gane, ba ƙaramin faɗa nake sha a wajen Mama ba, ƙawaye ma suna ta ganin baikena, ni kuwa ko a jikina don ji nake indai Sadam zai yarda da ni ya yi farin ciki da ni na wuce wajen. Zuwa gidan biki ko na 'yan'uwa sai wanda ya ga dama yake barina, ballantana na ƙawaye, haka kowa zai tafi, a bar ni ni kaɗai a gida, kuma sam ba na damuwa, Anisa ƙawata ce kuma 'yar'uwata, amma lokacin aurenta haka ya hana ni zuwa wajen dinner, ranar na yi kuka, musamman na gorin da na sha a wajen 'yan'uwa, haka aka dinga caccake ni, ana tsinewa soyayyar tamu, kuma a daren sai da ya zo zance, saboda ma ya tabbatar da ban je ɗin ba, yana ganin fuskata babu walwala shi ma ya haɗe tashi fuskar, ya shiga yi mini faɗa yana cewa"Sayyada saboda na hana ki zuwa wajen wannan shirmen shi ne za ki ɗauki fushi da ni? To ko da na hana ki zuwa ai umarni ne na ba ki, kina da damar bijirewa, tun da ban ɗaure ki ba, yanzu ma ki tafi ai ba ki makara ba, ban yi miki dole ki bi umarnina ba, amma kin san sharaɗin da soyayyarmu ke saƙale da shi ko? Idan kin ga kin zaɓi rabuwar fine!". Daga haka ya bar ƙofar gidanmu, na kasa bacci sai da na kira shi, ya ƙi ɗauka duk nacina, haka ita ma Anisa na dinga kiranta ta ƙi ɗauka, sai da ta yi mini massage sannan na haƙurwa, cikin saƙon take ce mini, tun da na zaɓi wani ɗan iska a kanta kar na sake nemanta, gobe ma ba ta gayyatata, don kar na je ya tsine min na bi duniya, na share hawaye a fili na furta"Ba za ku gane ba". Washegari da sassafe sai ga kiran shi, na ɗauka muka gaisa sama-sama, ya ce"Kin tafi gidan biki ko kina gida?" Na ce"Ina gida". Ya ce"To ki je, amma ki tabbata a gidanku kika yi sallar isha'i, duk wani shiririta da shirme da za ku yi kar ki sake ya wuce magriba, ki koma gida zan zo". Kamar zan yi kuka na ce"Amma fa akwai kai amarya, kuma Mama ta ce yau a can zan kwana, tun da wajen kai amaryar za a iya kai wa dare". Ya ce"Ni dai ga abin da na faɗa miki nan, ra'ayinki ne ki ji ko ki yi watsi da shi". Daga haka ya kashe wayar, na runtse ido ina jin kamar zan yi ihu, na rasa manufar wannan takunkumin da yake saka min, mutane suna yawan faɗa min idan mun yi aure ba ƙaramin kulle zai yi mini ba, ana ta nuna min takaicin da matar kulle take ƙunsa, amma ni gani nake indai mijina yana sona yana faranta mini muna zaune lafiya kuma zai ɗauki duka ɗawainiyata mene ne don ya yi mini kulle? Idan aka cire wannan dokokin da yake kafa min wallahi yana da daɗin sha'ani ya iya nuna soyayya da kalaman kulawa, a takaice dai gani nake ni ce na fi kowa dacen mijin aure. Ban ajiye wayar ba na ji shigowar saƙo, na duba na ga alert ne daga gare shi, na dubu hamsin, wani saƙon ya sake shigowa, na karanta faɗa min yake yi kuɗin gudunmawa ne na bawa Anisa, na tura masa da saƙon godiya, anko kala biyu aka fitar a bikin, kuma duka shi ya siyo min, ya kawo min a ɗinke kowanne da kalar takami da jaka da zai dace da shi, har da mayafai da set ɗin sarƙa mai kyau sosai, sannan ya haɗo min da dubu goma ya ce na yi liƙi, ban taɓa kuɗin ba, Baba na tambaya ya cika min na siyawa Anisa wani Jug me kyau na bata. Mama ta tafi gidan bikin tun asuba, sai ƙannaina da suke gab da gama shiryawa, dama umarni nake jira tun da na samu izini ni ma tuni na tashi na shiga wanka, na ce su jira ni, muka tafi tare, Na samu Mama na faɗa mata zancen kuɗin da ya ba ni na bawa Anisa, ta ce na ba ta dubu ashirin na bawa babarta talatin ɗin, na fita na je na ciro na bawa Umma na ce inji Sadam, nan fa aka dinga jinjina ƙoƙarinsa ana godiya, har na ji daɗi a raina, ya kankaro min mutunci. Na samu Anisa a ɗakinta cikin ƙawayenmu na makaranta, ta kalle ni ta kau da kai, na faɗa jikinta ina dariya da faɗin"Allah Ya huci zuciyarki". Da ƙyar ta sauko daga fushin, na ciro kuɗin na ba ta na ce inji Sadam, ta taɓe baki ta ce"Ai ni ko miliyan zai ba ni bai burge ni ba, kuma ba na so ki mayar masa". Na sauke numfashi ina tunanin ko ya za ta ji idan ta san ba zan je kai amarya ba? Kafin dai yamma ta yi ta saki jiki da ni, ta karɓi kuɗin har ma ta yi masa godiya ta wayata, kafin mu yi sallama ya sake jaddada min bayan magriba na dawo gida, na ce to, ai kuwa ana idar da sallar magriba na zame daga cikin 'yan biki na shiga ɗakin Umma na haye gado na lulluɓa da mayafina, kowa ya shigo sai ya tambaya sai na ce ba ni da lafiya, a dole Mama ta saka ni a gaba muka koma gida, raina babu daɗi saboda na so a ce na raka ƙawata ɗakinta. A haka muka cigaba da soyayya, yana nan yana kafa min dokoki ni kuma ina ta biyayya saboda gudun ɓacin ransa, idan na kuskure na ga tijarar da har sai na yi nadamar aikata laifin. Ko da wasa wani saurayi ya tsayar da ni a hanya ce masa nake ni matar aure ce, don kada ma tsautsayi ya sa a ce masa an gan ni da wani na shiga uku. Kwanci-tashi aka samu wata biyar da saka rana, arenmu ya rage watanni uku, a lokacin ne kuma Sadam ya fara fito mini da wasu sabbin halaye wanda na kasa gane musu, zuwa lokacin ya siya min babbar waya muna yin chatting, kuma mun fi yin na dare, saboda ya ce sai daren yake da lokaci, ya fara da tura min stickers na kiss da hug, da na nuna ba na so sai ya nuna min ba komai ba ne, ni kuma sai na yarda da babu komai ɗin, tun da ba wani tsaraici ba ne ake bayyanawa, gaba-gaba kuma sai ya fara tura min ta romance, babu kunya sai ya turo min hoton ƙinjin mace, har ma ya dinga tambayata nawa irin wanne ne? Tun ina ƙin amsa masa har dai na fara, saboda gudun ɓacin ransa, kuma yana maimaita min don yana sona ne yana tare da ni, wai idan bai tura min ba wa nake so ya turawa? Sai ka ce dole aka yi masa sai ya turawa wata. A ranar da ya fara tura min blue film hankalina ya tashi, saboda ban taɓa kalla ba ko da wasa, kuma na kasa jurewa har sai da na faɗa masa ba na so kar ya sake tura min, kashe wayar ma na yi sai da na yi kwana uku ban kunna ta ba, har ji nake yi kamar zan yi zazzaɓi, a cikin kwanaki ukun bai zo ba, a rana ta huɗu na kunna wayata ban ga saƙon shi ba, ban sani ba ko ya kira ni, gaskiya ya ɓata min rai kuma na fara zarginsa ma, idan ba yana yawon bin mata ba waye yake tura masa? Wata zuciyar take ƙila ɗakkowa yake yi a internet, ina kallon shi online bai yi min magana ba, sai na kasa jurewa ni na yi masa sallama, ya amsa ya ce lafiya? Na ce lafiya ƙalau, sai ya danna voice note ya ce min"Sayyada ba lafiyar jikinki nake tambayarki fa, tambayar dalilin yi min magana nake yi". Na ce"Yanzu sai da dalili zan yi wa mijin da zan aura magana?" Ya ce"To ai ba ki ɗauke ni a matsayin wanda zai aure ki ba, ban da haka kawai don na tura miki vedio shi ne za ki kashe waya? Kenan idan da zan ce ki zo ki taya ni wuni ba za ki amince ba ko?" Na yi shiru na rasa me zan ce masa ma, amma na shiga fargabar me Sadam yake nufi da ni? Ya sake yin voice ya ce"Na rasa irinki wallahi idan kina wani abu kamar haihuwar ƙauye, ban da shirmenki mene ne a cikin wannan? To gaskiya ni ba zan iya soyayya da mace irinki ba, ballantana kuma aure, don irinki idan mutum ya aure ki ma takaici zai kwasa wallahi, don haka kina da zaɓi guda biyu, ko ki koyi yadda za mu dinga gamsar da juna ta haka ko kuma a fasa auren nan kawai, sai ki je ki nemi ustaz ki aura tun da na ga ni kallon ɗan iska kike yi mini". Kamar zan yi kuka na ce"Ni fa ba haka nake nufi ba". Ya kira ni a waya, ina ɗauka ya ce"Ki buɗe baki ki yi mini bayanin me kike nufi? Wane kallo kike yi mini?" Na ce"Ba komai wallahi, kawai dai ni na tsorata ne, ba na son gani". Sai ya sanyaya murya ya ce"To me kike so?" Na ce"Da dai za ka daina turo min". Ya ce"Kina so na turawa wata kenan ko? Idan ba mu saba da wacce zan aura ba tun yanzu sai yaushe? Ko so kike sai bayan auren na dinga fama da koya miki abubuwa? Ni ba haka na tsara ba, amma ba zan yi miki dole ba shi yasa na ba ki zaɓi". Ya kashe wayar, a ranar na kasa bacci ina ta tunani na san dai haramun ne, amma da ya dinga tsara ni da kalaman yaudara, da na barazanar fasa aurena sai na amince, sannu a hankali muka saba da wannan mummunar ɗabi'a, tsakar dare wani lokacin bayan na yi bacci na farka, wataran kuma ba na yin baccin sai na jira shi, zan tashi zaune mu yi ta dirty chat, yanzu na saba da kallon vedion, kuma idan na kalla ina shiga wani yanayi sosai na buƙatuwa, yadda muke yi idan ya turo bayan na gama kalla sai ya ce mu yi sharhi a kan vedion, tun ina jin kunyar cewa komai har na saba na saki jiki, a hankali Sadam yake faɗaɗa min sha'awata, ta kai har na matsu a yi auren. Daga wannan kuma sai ya fara kwaɗaita kasancewarmu a zahiri, a nan ne dai na tirje duk kuwa ni ma zuwa lokacin ina jin sha'awarsa sosai, duk kalaman yaudara da ya dinga yi mini na ƙi yarda da shi, ya yi fushin ya gama ya dawo duk ban yarda ba, don na san wannan zina ce, ba shi da wasu kalaman da zai yi amfani da su wajen canza kalma, ni kuwa ba na fatan na aikata zina a rayuwata. Daga baya ya bar yi min zancen, sai dai muna nan tare a waya, aurenmu ya rage wata ɗaya, lokacin har an fitar da anko 'yan'uwa ana ta yi, ya ce Momynsa ta ce na je na gaishe ta, tana so ta gan ni saboda za su haɗa lefe, na ce masa zan tambaya a gida idan za a bar ni, ya ce ba sai na tambaya ba, saboda idan na tambaya za a iya cewa sai na je tare da ƙanwata, ita kuma Momy ba ta son haka, zan yi musu ya dakatar da ni da faɗin"Kin ga Sayyada idan fa ba za ki je ba babu dole, ai mahaifiyata ce dama ban ce ki kalle ta a matsayin uwa ba, sai dai kuma ki sani ba ni da kamar Momy a duniyar nan, duk macen da za ta nuna ba ta ɗauki maganar uwata a bakin komai ba wallahi ban ga amfanin cigaba da mu'amala da ita ba". Da sauri na ce"Ni fa ba da wata manufar na faɗa ba, shikenan yaushe zan je?" Ya ce"Ko gobe ma". Na ce"To zan tambayi zuwa gidan Anisa daga can sai na wuce ko?" Ya ce"Allah Ya kaimu". Washegari kuwa na je gidan Anisa tun safe, na wuni a can, ana yin sallar la'asar, na tafi, muka haɗu da Sadam a titin unguwar, ya ɗauke a motarsa muka kama hanyar gidansu, babban gida ne sosai, don iyayen shi masu rufin asiri ne, ya shiga da mota cikin gida, muka fito, gidan part biyu ne, na yi zaton babban part ɗin za mu shiga, sai na ga mun nufi ƙaramin, ya buɗe da mukullinsa muka shiga, falo ne madaidaici, sai sai ɗakuna guda uku, na zauna a kujera ina raba ido, gabana yana faɗuwa, saboda zan gana da surukata, ya fita, babu daɗewa ya dawo da drinks da snacks ya ajiye min, ya ce "Sorry babu kowa a gidan fa". Gabana ya faɗi na ce"Kamar ya?" Ya ce"E yanzu na shiga na ga ba kowa, sai na kira ta take ce mini ta tafi asibiti dubiya, wai ƙawarta aka kwantar, kuma na san za ta iya kaiwa dare ba ta dawo ba". Na ɗauki jakata na miƙe na ce"To gaskiya tun da hakane kawai zan tafi gida, wani lokacin sai na dawo". Ya ce"To jira na ɗan watsa ruwa sai na kai ki". Na zauna a tsorace, saboda yadda nake jin salon tantirancin Sadam a waya dole zan ji tsoron keɓewa da shi mu biyu a gida, har ya tafi ya dawo ya ce"Ko za ki taya ni wankan?" Da sauri na ce"A'a, don Allah ka yi sauri kar Mama ta ga na daɗe". Ya yi murmushi ya ce"Amma ai za ki taya ni shafa mai ko?" Na sunkuyar da kai ban ce komai ba, zuciyata tana ta bugu, ya shiga ɗaya daga cikin ɗakunan dake falon, don tsoro ko ruwa kasa sha na yi, saboda zarginsa kawai nake yi, kar ya zuba mini wani abu a ciki na sha ya cim ma buƙatarsa a kaina, sannan na fara tunanin karya yake yi dama ya san Momyn ba ta nan, so yake kawai ya yaudare ni. Ina nan zaune da zulumi na ji yana ƙwala min kira daga cikin ɗakin, na daga murya na amsa, ya ce"Zo mana". Gabana ya faɗi, na ce"Na'am me ka ce?" Ya ce"Zo ki ga wani abu". Na ce"Don Allah ka zo ka mayar da ni gida, bai kamata na shiga ɗakinka ba fa". Na ji motsin buɗe ƙofar ɗakin, ina juyawa na gan shi daga shi sai boxer, ya nufo ni, kafin ya ƙaraso na tashi na ɗauki jakata ina cewa"Ni zan tafi kawai sauri nake yi". Ya ƙaraso ya riƙe hannuna, da irin muryar nan ta cikin waya ya ce"Babyna, kenan da kike cewa kina kewar kasancewa da ni duk na ƙarya ne? Tun da ga ni yanzu mun samu dama me zai hana mu farantawa junanmu?" Ƙwalla ta kawo idona na ce"A'a don Allah, mu bar wannan har sai mun yi aure". Nan ya tisa ni a gaba da zantukan yaudara da daɗin baki yana nuna min ba komai ba ne wannan, wanda ba su da tabbacin za su auri juna ma suna yi ballantana mu da kwanaki ya rage aurenmu, bai ƙyale ni ba har sai da na amince na shiga ɗakin, ya yi yadda ya so da jikina, sai da ya nemi wuce gona da iri sannan na lura ni ma na shagala da yawa, na farga na taka masa burki, bai yi fushi ba sai ma godiya da yake ta min yana nuna min kulawa da soyayya, ya saka na yi wanka shi ma ya sake yi, sannan ya mayar da ni gida, jikina duk a sanyaye ina ta tsarguwa, gani nake kamar duk wanda ya kalle ni zai ga abin da na aikata liƙe a goshina. 08028966015 [27/09, 7:35 pm] Sadiya Abdulrazak: A sanyaye na shiga gida da siyayyar da ya yi mini a hanya, na miƙawa Mama kamar yadda na saba na ce inji shi, ta ce"A ina kuka haɗu? Ko shi ya kai ki gidan dama?" Na ce"A'a, yanzu zan shigo gida na gan shi, sai na ce masa kaina ciwo yake, shi ne ya ba ni ya tafi". Ta ce"To ciwon kai kuma? Ki ci abinci ki sha magani, kar dai ki kwanta sai kin yi sallah, ya Anisan take?" Na ce"Lafiya lau, tana gaishe ku". Na shiga ɗaki na kwanta, gabana sai faɗuwa yake yi, ina ta hango yadda kasancewarmu ta faru, na rasa ma me nake ji, Allah Ya sa ni ba da son raina ba ne, sai da aka fara kiran sallah na fita na yi alwala na yi sallah, na kasa cin abincin ma, ballantana magani dama lafiyata ƙalau babu ciwon kan, na kwanta lamo a katifa ina ta tunani, fatana dai Allah Ya sa kar Sadam ya sake neman mu aikata wannan abun, da daddaren mun yi waya da shi, amma na ce masa ba ni da lafiya, don haka ba mu yi irin chart ɗin da muka saba ba. Amma washegari muka ɗora daga inda muka tsaya, har ma yana yi min sharhin kasancewarmu, ni ma kuma a hankali sai nake jin daɗi idan na tuna yanayin, don haka a tare muke yin sharhin, kuma har ma ina jin ina ma mu ƙara kasancewa haka, amma fa idan mun yi aure nake nufi. Haɗuwarmu ta biyu gidan yayarsa ya ce za mu je, abun mamaki bai sake yi mini zancen zuwa gaida Momy ba, nan ma dai ƙarya na yi da zuwa gidan su wata ƙawata, ya zo ya ɗauke ni a hanya, wannan dai kai tsaye ya faɗa min ba gidan yayarsa za mu je, don kasancewa da ni yake yi, don haka hotel za mu je, hankalina ya tashi na ce"Hotel? Sai ka ce wata karuwa? Don Allah ka rufa min asiri, wallahi ba zan iya ba, don Allah ka mayar da ni gida, sati biyu fa ya rage aurenmu, muka yi haƙurin watanni masu yawa sai na sati biyu ya gagare mu?" Nan take ya ɓata rai sosai, ya ce"Shikenan ki je kawai, na gode, tun da ni ba ni da wata alfarma a wajenki a matsayina na wanda zai aure ki". Na fara hawaye ina tunani,ko a hasashe ban taɓa tunanin zuwan ranar da zan je hotel tare da saurayi da nufin aikata masha'a ba, a wannan lokacin dai ban yarda ba, na buɗe murfin motar na fita, ina saka ran ko da za mu zauna yana fushi da ni ba zan yarda ba, tun da sati biyu ya rage auren ko bai huce ba har lokacin idan aka kai ni ɗakinsa zai huce, adaidaitasahun na shiga na tafi gidan ƙawar tawa da na yi ƙaryar zan je, fira muke yi amma hankalina ba ya jikina, ina can ina tunanin halin da yake ciki. Can na ji shigowar saƙo wayata, na duba na ga shi ne, da sauri na fara karantawa, "Sayyada wallahi kin ji na rantse ba zan iya auren wacce ba ta girmama ra'ayina ba, tun daga waje na bawa wacce zan aura umarni ta karya ina ga an yi auren? Ki sani a yau na yanke hukuncin fasa aurenki, kuma wallahi da gaske nake, ba zan dai fito ƙarara na ce na fasa ba, amma zan ta ɗagawa har a gaji a san cewar na fasa ɗin, don haka na ƙara watanni uku a yau". Tsoro ya kama ni, zuciyata ta yi rauni na fara tunanin anya Sadam don gaskiya yake yi mini kuwa? Ban yarda da gaske yake ba, sai da daddare da Baba ya yi baƙi, bayan sun tafi ya zaunar da ni yake ce min iyayen Saddam ne suka zo, kuma sun nemi a ƙara masa watanni uku, don bai gama shiryawa ba, a ranar na ci kuka, haka na kira shi ina kuka, ni gani nake abun kunya ne 'yan'uwa da ƙawaye sun gana yin anko da shirin aurena kuma su ji an ɗaga saboda bai shirya, na kira shi na dinga yi masa kuka, shi kam ko a jikinsa, ƙarshe dai na ce na amince, ya ce ma ba ya so, sai kuma bayan kwana uku ya yarda muka haɗu, amma ya ce sam ba zai yiwu ya janye ɗagawar ba har sai ya ga gudun ruwana. Tun daga lokacin muka jone a wannan sabgar, mun yi nisa sosai, bayan zuwana gidan na farko na sake zuwa sau uku, duk ranar da babu kowa a gidan sai ya kira ni na je gidan, mai gadi dai ya san da zuwana, amma ina tunanin ko tsoron tonawa Sadam asiri yake, ko kuma yana ba shi cin hanci ne, daga baya ma sai ya siya katifa ya saka a gidan shi, muke zuwa can, an gama ginin gidan komai tsaf, shi yasa nake mamakin dalilin da ya sa ba za a yi auren a wuce wajen ba. Lokacin da auren ya rage saura wata ɗaya Saddam ya shigo min da babbar buƙatarsa, ya nuna yana buƙatar kusantata romance ya daina gamsar da shi kawai daurewa yake, kuka na saka masa da roƙon a bar wannan maganar, ya nuna min ba komai ba ne tun da dai aure za mu yi, dama abun nashi ne, don ya nema tun yanzu ba zai zama matsala ba, da na nuna ban yarda ba sai ya ce zai fasa auren ko kuma a ƙara ɗagawa, ni kuma a lokacin wallahi wata irin ƙaunarsa nake yi, ko ɗagawa ba na so a yi ballantana a kai ga fasawa, ga shi ni ma ya sabar min da romance ɗin, tsananin sha'awar shi tana neman kassara ni, shi yasa na matsu a yi auren. Ban san da gaske yake ba sai da Baba ya kira ni a wani dare, ransa a ɓace yake tambayata abin da saurayina yake nufi, jikina ya fara rawa fa na ji wai jiya ya ce sai dai a ƙara ɗaga auren nan, a ƙara wata biyu ya zama saura wata uku a maimakon wata ɗaya, Baba ya ce ya gaji, idan bai shirya ba na watsar da shi na bawa wani dama a yi da shi, wallahi ranar tashin hankalin da na shiga Allah kaɗai ya sani, na ci kuka na gode Allah, na gaji da gorin da ake yi mini na wannan ɗage-ɗagen auren da ake yi, wasu har suna cewa kuɗin ne ba shi da shi, alhalin ni dai ban ga babu a tare da Sadam ba, maimakon na yi karatun ta nutsu na gane Sadam jikina yake so ba ni ba, amma ina, na kasa fahimta, sai nake ganin laifina ne da na ƙi bin umarninsa, don haka na amince da sharaɗin ba za a sake ɗaga auren ba, ya ce ya amince. Na yi ƙaryar zuwa wani gidan, ranar muka haɗu a gidan shi, gabana yana ta faɗuwa, shi kuma Sadam yana ta rawar jiki da zumuɗin kasancewa da ni, irin wanda ango yake yi a daren farko, a ranar, a wannan gidan, wanda dai ya kasance gidan aurenmu a yanzu , a cikin ɗakin da yake nashi ne a yanzu, a kan ƙaramar katifa da filo guda ɗaya Sadam ya samu nasarar shiga hurumina, ya kawar da budurcina, ya mayar da ni cikakkiyar mace, na sha wahala daidai gwargwado, na ci kuka, haka ya mayar da ni gida wajen bayan isha'i, inda a ce Mama ta mayar da hankali sosai a gare ni za ta ga yadda tafiyata ta canza, duk da ina ta daurewa ina ƙoƙarin haɗe ƙafafuna, na kuma daure na ci abinci na yi sallah na kwanta, amma da safe na tashi fuskata a kumbure saboda kukan da na ci, idona sun jawur, ga shi na kasa haɗe ƙafata na yi tafiya kamar yadda na saba, da safen dai Mama tana ganina gabanta ya faɗi ta shiga tambayata mene ne ya same ni? Na ce mata ciwon kai nake yi da zazzaɓin, don kuwa da zazzaɓin na kwana, da yake lokacin sanyi ne, sai ta ce sanyi ya kama ni, shi ya kumbura min fuska, haka dai aka siyo min maganin zazzaɓi da ciwon kai na sha, na yi jinyata ni kaɗai, sai Sadam da yake yi mini sannu a waya sosai, tare da alƙawarin ba za a sake ɗaga aurenmu ba. Sati ɗaya da faruwar haka ya sake nemana, ya kalamance ni har na sake amincewa da shi muka haɗu, tun daga lokacin kuma shikenan, ya zamana duk sati sai ya neme ni sau biyu, ni ma yanzu abun har ya fara yi mini daɗi. Na sakankance, muka saba da Sadam sosai kamar wasu ma'aurata, a haka har lokacin bikin ya sake zuwa, ya rage saura sati biyu, shiru ba a kawo lefe ba, ga shi a wannan karon Baba ya ce indai aka sake ɗagawa to ya zare hannunsa a lamarin auren gabaɗaya, kullum cikin fargaba nake, duk da na san dai ina bin shi a yadda ya ce, sanda aka shiga satin bikin aka yi masa zancen lefe, sai ya ce a yi masa haƙuri a ɗaga auren zuwa wata ɗaya, nan take Baba ya ce sai dai a fasa, Sadam ya ce ba fasawa ya yi ba, yana ta ba da haƙuri ya tafi, a daren nan na ci kuka, na dinga kiran wayarsa ba ya ɗauka. Washegari tun safe Baba ya wakilta abokansa da yayansa ya ba da kuɗin auren da Sadam ya kawo a mayar da shi gidansu, abun mamaki da tashin hankali ne ya faru sanda suka ƙarasa gidan, domin iyayen Sadam uwa da uba cewa suka yi babu wanda ya san yana neman aure, ƙarshe dai na taƙaice muku labari Sadam iyayen bogi ya samu suka kawo masa kuɗin aure, ranar na ga tashin hankali, Baba ya fusata sosai, ya kira Sadam a kan ya zo ya karɓi kuɗinsa ya ƙi zuwa ya ce ya bar min, ban gama tsinkewa ba sai da ya yi mini massage ya ce na yi haƙuri mu haƙura da juna kawai, har ya ƙara da faɗin babana ba shi da kirki, shi kuma ba zai zauna a wulaƙanta shi ba, kiran duniyar nan ya ƙi ɗaukar waya, ni dai ranar a asibiti na kwana saboda zazzaɓi ne ya rufe ni ruf. Sai da na yi kwana uku a asibiti aka sallame ni, da na dawo gida babu zazzaɓin amma fa an kasa samun kaina, gabaɗaya na rikice, Sadam ya daina ɗaukar wayata gabaɗaya, duk na rame na ƙare, abinci ma yafita kawai nake, abu biyu ne ya haɗar min, ga zafin rabuwa da shi, ga kuma tunanin na riga na ba shi kaina ya gama buɗe ni, me zai faru idan na auri wani ba shi ba? Idan ya tambaye ni game da yadda ya ji ni kamar bazawara me zan ce masa? Auren wanda ya lalata ni shi ne kawai mafitata, ko da kuwa zai sake ni a sati ɗaya, duk wanda ya sake aurena daga baya ai ya san dama sunana bazawara, bazawara kuwa kowa ya san hanya ce daga Kano har Maiduguri. Kullum a kwance nake kamar ruwa, tun Mama tana kyarata da yi min faɗa a kan yadda na kasa mantawa da Sadam har ta daina, ta fara jana a jiki tana yi min nasiha da nuna min Allah zai kawo min wanda ya fi shi, amma inaa! Duk da haka na ƙi kwantar da hankalina, wallahi ban san abin da ya sakawa Mama zargina ba, kawai wataran sai ta zaunar da ni take tambayata ko dai Sadam ya taɓa sanina a 'ya mace? Ko na ba shi jikina? Na fara kuka ina girgiza mata kai alamar a'a, ba ta sake cewa kowa komai ba, sai washegari da safe ta ce na ɗauki hijjabina na fito, na ce"Mama ina za mu je?" Ta ce"Siyar da ke zan yi". Na ja bakina na yi shiru na saka hijjabin muka fita, muka shiga adaidaitasahun, ba mu tsaya a ko'ina ba sai asibiti, ban san bayanin da Mama ta yi musu ba, kawai dai na ga wata Nurse babbar mace ta kira ni, ta zaunar da ni take tambayata a tsanake wai lokacin da muke soyayya da saurayina wani abu ya taɓa shiga tsakaninmu ne? Na ce mata a'a, ta ce na faɗi tsakanina da Allah, na dinga hawaye har da rantsuwa ta, na ce wallahi babu komai, aka yi min gwajin ciki da na HIV, kowanne nagative, ta ce to na hau gado za ta duba ni, gabana ya yanke ya faɗi, na fara roƙonta kar a yi haka wallahi lafiya ƙalau nake, sai da ta ɓata rai sannan na saddaƙar na hau gadon bayan na cire pant ɗina na ajiye, da ta duba ba ta ce min komai ba, amma a gabana ta yiwa Mama bayanin ba daɗe da sanin namiji, a ranar na ci kuka, don kukan da Mama ta yi ya tada hankalina sosai, haka muka koma gida ni ina gursheƙen kukan nadama, ita tana share hawaye. A wannan ranar dai na ga ta kaina, domin Baba bulala ya saka ya zane ni, da ƙyar aka ƙwace ni, kuma ya ce ya zare hannu a lamarina gabaɗaya, babu shi babu ni, cewa ya yi ma sai dai na bar masa gidansa, duk yadda aka ba shi haƙuri ƙin haƙura ya yi, sai gidan yayansa na tattara na koma wato mahaifin Anisa. 08028966015 [28/09, 7:32 pm] Sadiya Abdulrazak: Yayan babana shi ne ya tsaya min tsayin daka, bayan ya gama yi min nashi faɗa da nasihar, ya ce hannunka ba ya ruɓewa ka yanke ka yar, sannan ba za a bar Sadam ya ci bulus ba, ya zama dole ya aure ni, shi ya shige gaba ya je gidan su Sadam ya sanar da su ya riga ya lalata ni, don haka auren nan babu fashi, idan kuma ya ce ba zai aure ni ba to za a yi ƙararsa a kan lalata min rayuwa da ya yi, shi ne mahaifinsa ya ce ba damuwa zai aure ni, yayinda mahaifiyarsa ta yi tsallen baɗake ta ce ba zai auri mara tarbiyya ba, aka dinga kai ruwa rana, ƙarshe dai aka fi ƙarfinta, aka sake saka ranar aure sati biyu masu zuwa, Baba ya ce ko ya shirya ko bai shirya ba za a ɗaura idan ma a kafaɗa zai yi yawo da ni sai dai ya yi, da aka sanarwar babana sai ta ce babu ruwan shi fa a magana, kuɗin kayan ɗaki dama ya daɗe a wajen kafinta kuma aka yi sa'a Baba bai karɓe ba, kayan kitchen ɗina ma tuni an gama haɗa komai, don haka ba a da matsala ta nan ɓangaren. Kuma wani abun mamaki Sadam shi ma ya amince da auren, bai nuna mini wani ɓacin rai ba, firarmu muke yi hankali kwance, sai yake nuna min shi fa dama ba auren ne ba ya so a yi ba, kawai dai ƙaryar da ya yi tun farko ne bai faɗawa iyayensa zai yi aure ba, ya sa shi fargaba, hakan ne ya ja komai, ni dai kawai bin sa nake da kunne, amma ina tsoracewa kaina kalaman da aka yi ta faɗa min na cewar ko an yi auren ba zan yi daraja ba a idonsa, ba na fatan hakan ta tabbata, bai kawo lefe ba, kuma ba wanda ya tambaye shi, saura kwanaki uku auren dai ya kawo kaya a ɗinke kala biyar, da takalma biyu jaka biyu, sai mayafai da sarƙa, ya ce na yi fitar biki. Haka aka ɗaura auren, ba a yi wani taro ba, sai 'yan'uwa na kusa ne kawai suka zo, aka je aka jera min kayana a gidan, an tarar ma ya zuba kujeru masu kyau, kayan kallo da babban firji a falo, haka ɗakinsa ma ya saka gado, aka jera sauran kayan a ɗakunan da suka yi saura, a daren da za a kai ni ɗakina Maman Anisa ta saka ni a gaba zuwa gidanmu don na nemi yafiyar iyayena, Mama ta ce ta yafe min ita dama ba ta ƙullace ni ba, yayin da Baba ya ce ba zai sake cewa komai a kaina ba, amma dai na sani ya bar wa Sadam ni har abada, kar na sake na ce zan zo gida na kwana ko da ziyara ce ballantana yaji, idan zai dinga yankar naman jikina yana ci kar ma a faɗa masa ballantana a yi tunanin zai ɗauki mataki, tun da har na iya yin watsi da tarbiyyar gidansa to na je na rayu da wanda na zaɓa rayuwa ta har abada. Na ci kuka a ranar kamar babu gobe, na san na yi laifi, ban yi wa iyayena adalci ba, amma a ganina ko ma me na yi bai kamata Baba ya yanke wannan hukuncin mai tsauri ba a gare ni, tun magriba kowa ya watse, wajen ƙarfe tara Sadam ya zo shi kaɗai ya ɗaukata duk an yi zaton ma dai gobe ne kai amaryar, tare da Baban su Anisa muka tafi ni ina bayan mota shi yana gaba, sai da ya raka ni har ɗakina, ya haɗa mu ya yi mana nasiha, sannan Sadam ya mayar da shi gida, ina zaune ina ta share hawaye ya shigo gidan, hannunsa ɗauke da ledoji, ya ajiye, sai na ga jikinsa a sanyaye fuska babu yabo babu fallasa, sam babu wani zumuɗi na angwaye, ya zauna a kusa da ni muka yi shiru na ɗan lokaci, kafin ya ce"To Sayyada daga ƙarshe dai aurenmu ya tabbata, sai mu ce Alhamdulillah! Allah Ya ba mu zaman lafiya, Sayyada ina son ki, kuma ina fatan za ki cigaba da bin ra'ayina a komai, idan kika yi min biyayya a zamanmu na yi miki alƙawarin samuna yadda kike so, ba ana cewa wasu mazan mijin ta ce ba? To ni kam zan zame miki kan ta ce". Ni dai na kasa cewa komai, ya ce"Kin yi shiru, ko dai ni kaɗai nake farinciki da wannan ranar?" Sai na fashe da kuka sosai, na kwanta a jikinsa na riƙe shi na ce"Ni amana ce a wajenka, Babana ya ce ya zare hannunsa a lamarina ya sallama maka ni, ya ce ko yanka ni kake yi bai amince na koma gidansa ba, ballantana yaji, ziyara ya ce ba zan sake zuwa na kwana ba, Sadam kai kaɗai ne da ni a yanzu, ka dubi Allah ka yi mini adalci a zamanmu, ka yi wa iyayena adalci ka kula da ni, ko haka zai wanke musu ƙuncin da na saka musu a zuciyoyinsu, don Allah ka rufa min asiri mu bawa maraɗa kunya". Ya fara shafa bayana yana cewa"In sha Allah Sayyada zan yi iya yina na ganin na yi miki adalci, in sha Allah babu wanda zan bawa damar yi miki dariya, za mu zauna lafiya matuƙar za ki cigaba da yi min biyayya". Mun ɗan dade a haka kafin ya ɗago ni ya ce na je na yi alwala mu yi sallah, bayan mun idar ya miƙo min ledar da ya shigo da ita, na kai kitchen na juyo mana kaza a faranti tare da kofina, muka ci muka ƙoshi, raina duk babu daɗi, jiki a mace, shi dai ban san mene ne a zuciyarsa ba, bayan mun kammala ya shiga ɗakinsa ni ma na shiga nawa, na sake yin wanka, na saka rigar bacci mai ɗaukar hankali, tun da a yanzu babu wata kunya tsakanina da shi, na koma ɗakin nasa na tarar shi ma ya fito daga wankan, ya saka kayan bacci ya kwanta yana cewa na kashe hasken ɗakin, shiru na yi bayan na kwanta ina jiran ta inda Sadam zai fara taɓa ni ko ya matso kusa da ni kamar yadda na san zai yi wuya ango ya kasance a daren farko bai ko kai hannu jikin amaryarsa ba, amma sai na ji shiru, a zatona yadda yake mararina idan mun haɗu a yau da na zama mallakinsa zai yi fiye da kullum, sai na ga saɓanin haka, sai ni ce na ja na matsa kusa da shi, na kwantar da kaina a jikinsa, a haka bacci ya ɗauke mu. Da asuba ya tashi, ya tashe ni, sannan ya tafi masallaci, bayan ya dawo ya sake kwanciya, ni kuwa zaune na yi ina ta tunanin wannan sabuwar rayuwa da na shiga, ina kuma istigfari har gari ya waye, na tashi na shiga kitchen na haɗa mana abun karyawa, komai na kayan abinci akwai a store ɗin dake kusa da kitchen ɗin, ina kammalawa na gyara gidan sannan na yi wanka na yi kwalliya na je tashinsa, na same shi yana shiryawa, na yi masa murmushi na ce"Ashe ka tashi". Shi ma ya mayar min da murmushin ya ce"Na tashi, ai na makara ma, zan je wajen aiki". Na ce"Aiki? Ina alƙawarinmu da kai, na cewar za ka ɗauki hutun sati ɗaya idan mun yi aure?" Ya ce"Ban manta ba, abun ne ya zo babu shiri kin ga ai, ban kammala wasu ayyukan ba, ga shi Abba yana gari, idan ya ga ba na zuwa Company za mu samu matsala". Na marairaice na ce"Kuma ni kaɗai za ka bar ni a gidan?" Ya ce"Ki yi haƙuri, next zan ɗauki hutun sai mu huta". Ya kammala shirin ya fito, muka ci abinci na raka shi ƙofar falo ya tafi, na koma na yi wanke-wanke na kwanta ina ta tunanin yadda zaman aurena zai kasance. A ranar dai ya kusance ni, abun dai kamar yadda muka saba, amma bambancin ɗaya ne a baya idan mun gama zai ta yabo na, da nuna jin daɗinsa, yau kuma sam bai yi wannan ba, washegari ma hakan ce ta faru, mun kammala na fito daga wanka yake cewa"Ni wai Sayyada ko irin gyaran amaren nan ba a yi miki ba a gidanku? Ta ya zan ji ki yadda na saba jinki a waje?" Na yi shiru na ji duk na kunyata na muzanta, sai yanzu ma na tuna ya kamata na gyara jikina, amma ai a ƙa'ida buduruwa gyarata ake yi ba ita za ta nema da kanta ba, wata zuciyar ta ce min ai ke kin zubar da garinki shiyasa, kuma na yarda da hakan. A sanyaye na ce"Kenan ba wani daɗi da ka ji?" Ya ce"Ina fa daɗi abu salam? Dama haka ake amarya? Gaskiya ya kamata ki gyara ko ki ce a gyara ki". Na ce"To a yadda auren namu ya kasance wane ne zai yi tunanin gyara ni? Kuma yanzu kowa yana jin haushinta wa zan tunkara da batun gyara?" Ya ce"To ki san dai yadda za ki yi, don idan aka tafi a haka ni fa sam ban mori amarci ba, ji nake ga maganin nan ana ta tallansa, ki nemi inda za ki siya zan ba ki kuɗin". Na ce"To zan nema in sha Allah". Na kwanta jikina duk ba ƙwari, sai ya matso kusa da ni ya kwantar da kansa a jikina, saitin kunnena da shu'umar murya ya ce"Baby, don Allah ina neman wata alfarma". Na ce"Allah Ya ba ni ikon yi maka". Ya ce"Yanzu idan kin gyara jikinki sabuwar rayuwa za mu buɗe mu dinga shan amarcinmu daidai gwargwado, haka kuma ba zai yiwu ba muddin kika samu ciki, gaskiya dama ni a tsarina na fi so sai mace ta yi shekara ɗaya mu huta da juna sosai mun sake fahimtar juna mun ga tsara zaman mu sannan ta fara haihuwa". Gabana ya faɗi, na nutsu tsam ina ta auna kalamansa a raina, ya ce"Kin ga ba mu san da wane yanayi cikin zai zo ba, ƙila ki yi ta laulayi duk ki rame ki fita a hayyacinki kuma kin san idon danginki yana kanmu, yanzu sai a fara yi miki dariya ana zaton wahala kike sha a gidan, amma idan kika huta kika yi ƙiba muka sha soyayyarmu idan haihuwar ta zo ma sai mun fi marmarinta, amma ya kika gani?" Na ce"Amma anya babu matsala kuwa? Ni a ra'ayina ko haihuwa ɗaya ce na yi kafin planing". Ya ce"To ni dai ga yadda na tsara mana, idan kuma ke ce mijin ni matar sai ki yi naki tsarin". Ya janye jikinsa ya juya min baya, hawaye ya sakko min, Allah Ya jarabce ni da ƙin son ganin Sadam yana fushi da ni, a raunane na ce"Ni fa ban ce ban yarda ba, amma kamar wata nawa za mu yi planing ɗin?" Ya ce"Shekara ɗaya ma ya isa, indai kika bi umarnina Sayyada za ki ji daɗin zama da ni wallahi, na faɗa miki babu wata mace a waje da za ta sake ba ni sha'awa ballantana ma har na aure ta, saboda ni ma ina sane samun irinki sai an tona". Ya ce"Kin amince?" Na ce"Na amince, ina sonka mijina, so ne ya sa na aure ka, kuma zan yi ta maka biyayya a kodayaushe, fatana dai ka yi mini adalci a zamanmu, don Allah kar ka butulce mini, kar ka kawo wata cikin rayuwarmu ta rage mana farinciki, ba zan iya raba ka da kowace mace ba, kishi ne zai saka zuciyata ta yi bindiga". Ya ce"Na yi miki alƙawarin hakan ba za ta faru ba My Baby". Ya kashe ni da daɗin baki sosai har na daina fargaba na amince har zuciyata, washegari kuwa ya ɗauke ni muka je wani private hospital, amma na yi mamakin ƙaryar da ya yi musu, ya ce matarsa ce ni, haihuwata uku duk CS ake yi min ana ciro yaran babu rai, shi ne muke buƙatar na yi planing na samu hutu kafin samun wani cikin, kuma implant yake so a saka min, saboda an yi min allura ta saka ni zubar jini, ƙwaya kuma ba na jurar sha mantawa nake yi, haka na yarda aka saka min tsinke na shekara biyar, da zummar idan ya yi shekara ɗaya za a cire shi, Sadam ya dinga lallaɓa ni, a cikin kwana ukun da aka ce kar na yi aiki da hannun komai shi yake yi, har wanka yi min yake, sannan bai kusance ni ba, ya ce sai na gyara jikina. Anisa na tambaya inda ake siyan maganin mata, ta haɗa ni da wata mata ta ce kayanta suna da kyau sosai, na yi mata magana na ce ni bazawara ce zan yi aure ta yi min haɗi mai kyau, ta ce na kawo dubu ɗari za ta haɗa min komai har maganin sanyi ingantattu, na turawa Sadam account numberta, nan take ya saka mata kuɗin, a ranar kuma aka aiko min da kayan, na hau amfani da su ka'in da na'in. Kafin na yi rabin kayan ni kaina na ji canji a jikina sosai, ranar kuwa da ya dawo min shi ma ya faɗa ya ce sai yanzu ya san ni amarya ce, wannan gyaran da na yi ma ya ƙarawa zamanmu amarshi, daga nan muka sake sakin jiki da juna, muka cigaba da shimfiɗa rayuwar aurenmu cike da soyayya. Ƙalubale ɗaya shi ne ba ni da wata alaƙa da danginsa, sau ɗaya ya taɓa ɗaukata muka je gidansu, ai kuwa sai da na yi nadama, saboda yadda Momy ta yayyanka min maganganu ta ce kar ta sake ganin ƙafata a gidanta, ba ta sona, ba ta son aurenmu, ba ta alfahari da kasancewata matar ɗanta, kuma ba za ta taɓa yi min kallon suruka ba, na ma daina sakawa a raina ina da suruka indai ita ce, ina hawaye muka bar gidan, Sadam yana ta kwantar min da hankali, tun da kuma ban sake zuwa gida ta ba shikenan babu wani abu da take yi mini da nufin ƙuntatawa, kowa sabgarsa kawai yake yi, shi dai Sadam kullum sai ya je gidan, ina zuwa gidanmu, ina samun tarba daga wajen Mama, Baba ne dai sai dai kawai ya amsa gaisuwata fuska babu walwala, ban sake fira da Baba ba tun daga ranar da ya san na ɓarar da mutuncina. Haka rayuwar ta yi ta miƙawa, ko na ji kewar samun ɗa ko 'ya sai Sadam ya wanke min wannan tunanin, da soyayyarsa me tsayawa a zuciya, mun yi zaman lafiya sosai, har na tsayin shekara biyu, duk lokacin da na yi masa maganar cire tsinke sai ya ce mu ɗan ƙara lokaci, muna shiga shekara ta uku mahaifiyarsa ta fara saka mana ido da tambayar ƙalau nake kuwa? Me yasa ban haihu ba har yanzu, sai dai ya ce mata Allah ne bai kawo ba, ni mamaki ma ta dinga ba ni, tun da a ganina tun da ba ta sona ma ai ba za ta so ɗanta ya haihu da ni ba, a hankali ta fara matsawa da zancen rashin haihuwata, na ce masa to a cire mana kawai na samu cikin nan, firr ya ƙi, sai ya zamana ma indai ina so mu yi faɗa to na yi masa batun a ajiye planing ɗin nan, yanzu zai birkice min na kasa gano kansa, shi yasa na rabu da shi don na ga gudun ruwansa, ai kuwa ƙarshe na gani. A hankali na lura ya fara bawa wayarsa muhimmanci, ko fira muke yi hankalinsa na kan waya, sotari sai na yi bacci na barsa yana danna waya, ko tsakar dare na farka na same shi a falo da waya, da na so yin ƙorafi sai ya taka min burki da faɗin ban isa da na tsara masa rayuwarsa ba, shi ba lusarin namiji ba ne, na ja baki na yi shiru, sau ɗaya na taɓa ɗaukar wayarsa na duba, ai kuwa na ga yadda yake lalata da mata a waya, abun har ya ƙazanta, a ranar saura kaɗan kaina ya fashe, wani ɗan ƙaramin yaƙi aka yi a gidan, don birkice masa na yi na dinga hauka da ihu, shi kuma tun yana kare kansa har ya fara cewa ya yi ɗin na ɗauki mataki, nan fa zagi da gore-gore ya ɓarke a tsakaninmu, yana jifana da kalmar mara tarbiyya ni ma ina faɗa masa shi ne mara tarbiyya, ban taɓa ɗaga masa murya ba sai a ranar, don haka ya faffala min mari, wanda hakan bai kashe bakina ba, tun daga ranar kuma bakina ya buɗe, idan ya faɗa min baƙa ni ma sai na mayar masa, tun da na lura shi bai san halakci ba, na yi zaton irin sadaukarwar da na yi masa tun kafin aurenmu zai saka ya yi mini kara idan halin nasu na maza ya motsa, sai ya nuna min sabo da kaza ba ya hana yankata. LITTAFIN NAN NA KUƊI NE AKAN NAIRA 700, KAFIN NA GAMA FREE PAGES MAI SO ZAI SAKA 500, WANNAN DISCOUNT ƊIN NA 'YAN KWANAKI ƘALILAN NE, DON FREE PAGES SUN KUSA ƘAREWA. 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay 08028966015 [29/09, 6:07 pm] Sadiya Abdulrazak: Ban tashi sanin na yi ganganci ba, sai da na ga da gaske Sadam yanzu ba ya ta ni, kuma aurensa zai yi, duk yadda nake yi masa bambamin sai na cire tsinken jikina ya ƙi, a ganina wannan ai mugunta ce, kenan ni ya mayar matar ado, zai auro wacce za ta dinga haihuwa, shi yasa ƙarshe na ɗauki matakin da na ɗauka. A sanyaye ya shigo ɗakin, na sauke idona a kan shi, sai hawaye suka fara zubo min, ya ce"Ki fito ga likitan nan ya zo zai ga hannun". Ya juya ya fita, na tashi, na ɗauki mayafi na yafa na fita, bayan ya gama dubawa ya yi mini faɗan na daina yawan motsa hannun, bayan ya tafi na tashi zan koma ɗakin, Sadam ya ce"Sayyada, ki dawo ki zauna mana, ba fita zan yi ba, zan ɗan ɗauki hutun aikin saboda na kula da hannun naki". Na ce"Ba na buƙatar kulawarka, ka je ka kula da wanda suka damu da kai". Na wuce ɗakin, ya biyo ni, na hau gado na kwanta, shi ma ya hau gadon, ya kamo hannuna me lafiyar yana matsawa ya ce"Jikinki akwai ƙwarin da za ki iya karɓa ta? Ina buƙatarki". Takaici ya sake kama ni, na ce"A'a, sai dai ka yi min fyaɗe". Ya yi murmushi ya ce"Ai babu fyaɗe tsakanin mata da miji". Na yi shiru don magana da shi ma na so nake ba, ballantana na tsaya na shi hujjojin da zai tabbatar akwai fyaɗen. Na yi ƙoƙarin ƙwace hannuna ya riƙe ni tamau ya ce"Tashi ki sha maganinki". Ya fita ya ɗakko maganin da ruwa, yana cewa"Na haɗo miki shayi?" Na ce"Na sha a asibiti". Ya ɓallo maganin ya ba ni na sha, sannan na koma na kwanta, ya sanyaya murya ya ce"Kin ga Sayyada wannan zaman namu ba zai haifar mana da ɗa mai ido ba, ba na son rashin kunya da neman fitina, ke kuwa yanzu shi kika saka a gaba". Na ce"Sadam ni fa indai ba fasa auren nan ka yi ba wallahi ba wani abu da za ka faɗa min na saurare ka". Ya yi shiru na ɗan lokaci kafin ya ce"To shikenan Sayyada, zan saka a ɗaga auren zuwa wata uku, indai kika samu ciki a cikin wata biyu na yi miki alƙawarin zan fasa auren". Na ce"Da gaske". Ya ce"Na rantse miki zan fasa indai kin samu ciki nan da wata biyu zan fasa auren nan". Sai na ji hankalina ya fara kwanciya, na ce"In sha Allah zan samu, Allah Ya ba mu mai albarka". Ya ce"Amin, amma kin san samun ciki ba zai yiwu kina guduna ba ko?" Na ce"Na daina, dama ai don ina takaicin za ka yi auren ne shiyasa". Ya ce"Fine! Yanzu na matso kenan?" Na ce"Haba don Allah, ba ka ga halin da nake ciki ba ne? Ina laifin ma a bari zuwa sanda ciwon nan zai warke?" Ya ce"Shikenan, Allah Ya ba ki lafiya". Na amsa da amin, sai kuma ya ce"Don Allah ki yi min shikenan za mu zauna lafiya, kin fitini kanki duk kin rame, ba ki taɓa zuwa gida da zummar kina fushi da ni ba sai a wannan karon, don Allah ya zama na ƙarshe kin ji?" Na ce"Idan ka so zai zama na ƙarshen in sha Allah, zan yi bacci". Ya ce"A tashi lafiya" Ya fita ya bar min ɗakin. Tun daga ranar Sadam ya dage da kulawa da ni, kullum sai Mama ta kira ni ta ji lafiyata, don na faɗa mata ba ni da lafiya, amma ban ce mata ga abin da ya same ni ba, a yadda na lura duk ta yi zaton laulayi nake yi, har yanzu ba ta taɓa zuwa gidana ba, kuma ina zargin Baba ne ya hana ta zuwa. Bayan na warke muka cigaba da zaman lafiya da Sadam, kamar gaske ya rage yin chatting ɗin dare, yana ba ni lokacinsa kamar baya, a yadda ya ce min ya dakata da kula Safna har sai wata biyun ta yi an ga yadda zan kasance, sosai na hana idona idona baccin dare, rabin dare Sadam ya yi yadda ya so da ni, rabi kuma na raya shi da sallah, haɗi da addu'ar Allah Ya ba ni haihuwa mai albarka, sannan ina ta lallaɓa Sadam, ina kyautata masa, ado da kwalliya kuma na linka a kan wanda nake yi, bayan wata ɗaya ina ta addu'a da fatan Allah Ya sa kar na ga period ɗina, ai kuwa sai ga shi ya zo, ranar har kuka na yi, saboda a yadda nake sakarwa Sadam jikina wallahi ban yi zaton ba zan samu ciki a watan ba, ashe ba daga nan take ba, sai na tsananta addu'a, har sadaƙa nake kaiwa islamiyyar kusa da mu, haka nake turawa Mama kuɗi na ce ta sa a yi min sauka a islamiyya Allah Ya cika min burina, da ta ritsa ni da tambayar burin nawa na faɗa mata Sadam ne zai ƙara aure saboda ban haihu ba, yanzu kuma ga sharaɗin da laƙanya min, shi yasa nake fatan samunta ido rufe. Haka wata na biyu ya zo, ina ta fargaba wallahi har ramewa na yi, saboda abinci ma ba ni da nutsuwar ci yadda ya dace, watarana muna zaune da shi nake tambayarsa "Wai yanzu a ina kuka kwana da batun yarinyar?" Ya ce"Ai na faɗa miki sakawa na yi a ɗaga auren ko? Idan kuma ba ki samu cikin ba sai a yi a lokacin da aka saka tun farko, kin ga yanzu saura sati biyu kenan". Na ji na sare, saboda ban ga alamar ina da ciki ba, kuma a lissafi wani satin al'adata za ta zo, na ce"Don Allah ina neman alfarmarka". Ya zuba min ido bai ce komai ba. Na ce"Idan ban samu ciki a watan nan ba, ka dubi girman Allah da manzonsa ka ƙara min wasu watanni biyun". Ya ce"A'a, ko kwana ɗaya ba zan iya ƙara miki ba Sayyada, indai ba ki samu cikin nan ba shikenan kawai ki yi haƙuri a yi auren nan a wuce wajen, ni ban ga dalilinki na tada hankali fa ba ma, ba fa gida ɗata za ku zauna ba, tana gidanta kina naki, kuma ba wai zan canza miki don na yi aure ba, ƙalau za mu zauna idan kika so". Kamar zan yi kuka na ce"Ai ba zan iya zama da kishiya ba ne, me zan yi ka fahimci ba zan iya haɗa miji da wata ba? Kamar yadda na yi maka biyayya a baya na so abin da kake so, don Allah ka yi min alfarma ni ma ka ba ni dama ko da 'yar kaɗan ce, duk fa kai ne silar komai, da tuni na yi haihuwa biyu". Ya ce"Hmm! Allah Ya zaɓa abin da ya fi zama alkhairi kawai". Tun daga ranar bai sake tattaunawa da ni game da aurensa ba, ko maganar nake yi sai dai ya yi shiru, na ƙaraci kukana ba zai ce min ƙala ba, ana haka al'adata ta zo, tabbacin dai na karya wannan sharaɗin, ta tabbata ban samu ciki ba, hakan yana nufin auren Sadam sati ɗaya ya rage babu fashi. Na fara al'ada ranar Juma'a, ranar Asabar yake ce min"Sayyada, na lura kamar jiya kin fara al'adarki ta watan nan ko?" Na gyaɗa masa kai alamar e, na ce"Amma don Allah ka taimake ni ka ƙara min lokaci". Na ce"Ba zai yiwu ba, Sayyada ki yi haƙuri kawai ki ɗauki ƙaddara, Allah Ya sa hakan shi ya fi alkhairi". Na ce"Ta ya kishiya za ta zama alkhairi? Kishiyar da aka yi ta don a ƙuntata min? Sadam don gaskiya Allah ka sake ni". Ya ja tsaki ya ce"Wallahi Sayyada kukan daɗi ma kike yi, ta ya zan ta baki da lallaɓa ki kamar wata jaririya? To ki je ki tambaya ki ji, ki tambayi matan da mazan su suka ƙara aure, haka suke yi musu komai a tsanake suna kwantar musu da hankali? Wallahi samu kika yi ma" Na ce"Ai da ni da sauran matan ba ɗaya ba ne?" Ya ce"Ok ke da gwal aka sassaƙa ki ko?" Na ce"Ba halitta nake faɗi ba, halacci da sadaukarwar da na yi maka, azabar da ka gana min kafin ka aure ni". Ya ce"To Sayyada kin yi min halakci na butulce miki, a je a hakan sai me? Idan kin so ai kina iya rama butulcin, a iya sanina duk wani adalci da ya kamata na yi miki na yi, ko na ce ina kan yi, amma tun da kina ganin ban yi miki daidai ba to ki ɗauki mataki". Cikin kuka na ce"Ai matakin yana hannunka! Ka sake ni mana". Ya ce"Za ki iya sakin kanki ai ko?" Na ce"Kana nufin ka bar min igiyar sakin a hannuna?" Ya yi banza da ni ya fice daga ɗakin, babu jimawa ya dawo da akwati 'yar tsakiya, ashe dama tana cikin motarsa, na saki baki ina kallon akwatin, ya ajiye min ya ce"Ga kayan faɗar kishiya nan, an kai kayan lefen Safna tun sati biyu da suka ce, saboda dama na san ba samun cikin za ki yi ba, wannan tsinken wasu idan aka cire musu shi, sai sun yi wata shida kafin su samu ciki, duk da an ce akwai masu samu da zarar an cire, don haka gara ma ki kwantar da hankalinki, kawai ki cigaba da addu'a idan Allah Ya dube ki ya ba ki shikenna sai mu gode masa, idan sex ne ke saka a samu ciki ai da azabar da kika gana min cikin wata biyun nan sai kin samu cikin 'yan biyu, don haka na daina ɓata lokacina, kuma ki daina mafarkin zan sake ki, idan kika cigaba da cewa na sake ki wallahi wataran sai na fasa miki baki, shashasha kawai, za ki ga alert, sai ki yi ɗinki da shi". Daga haka ya shiga ɗakinsa ya rufe ƙofar da mukulli, ya bar ni tsaye ina kokawa da numfashi, sai da ƙyar na samu na daddage na rusa ihu, kuka kuwa ya ɓarke min, na tashi a haukace a buɗe akwatin, na shiga fito da kayan dake jere a ciki ina watsi da su a falon ina faɗin"Wallahi Sadam sai ka sake ni, ba zan zauna da kishiya ba!". Ko sake fitowa falon bai yi ba, na je na dinga buga ƙofar ɗakin nasa ya ƙi buɗewa, da na leƙa ta windo sai na hango shi a tsakiyar gado yana waya haƙoransa a waje, da alama yana cike da shauƙi, ni ya mayar mahaukaciya, na durƙushe a wajen ina ta kuka, na yi mai isata na ta shi na shiga ɗakina, da asuba ina jin dawowarsa daga masallaci na fita na tare shi a falo, na ci kwalar rigarsa zan fara sababi, ai kuwa ya fincike ya wancakalar da ni a ƙasa, na shiga zaginsa ina yi masa Allah Ya isa, ya dinga dukana ta ko'ina, har ƙafa ya saka ya dinga tattaka ni yana zagina shi ma da faɗin, tun da haukan na zaɓi a yi ai shi ma ya iya mu zuba mu gani, tass ya yi min jikina ya yi tsami sosai, ya shiga ɗaki ya yi wanka na fice daga gidan, takaici ya hana ni motsawa daga kwancen da nake ina yin kuka kamar marainiya. Sai da yunwa ta fara damuna sannan na tashi, siket ɗin jikina duk ya ɓaci da period saboda gumurzun da muka yi, don haka wanka na fara yi na gyara kaina, na shiga kitchen na ɗora indomi, na haɗa shayi, na karya, na sha maganin zazzaɓi don na fara jin alamaunsa, ciwon kai kuwa dama tuni ya dirar mini. Haka na wuni cikin ƙunci, da rana na yi girki ɗan kaɗan na ci na rage na dare, yau ko shara ban yi ba, kayan nan na faɗar kishiya a falon suka wuni a warwatse, na so na kai ɗakinsa na watsa su, sai na tarar ya rufe da mukulli, ina jin dawowarsa na koma ɗakina na kulle, sai ga shi bai ma neme ni ba, hakan kuma sai ya ƙara ƙona zuciyata, na rasa ta yadda zan nunawa Sadam son shi da nake yi ne ya sa ba zan iya haɗa shi da wata ba, amma shi ya kasa fahimta, ni dai na san zan iya mutuwa idan ya auri wata, shi yasa nake yin iya yi na, amma na lura nema ake a ci ni da yaƙi. Washegari sai ga Anisa ta zo gidan, ta tarar da ni kamar mahauciya, saboda yadda nake a firgice, ga falona har yanzu da kayan lefen a baje, har da akwatin, hankali tashe take tambayata abin da ya faru, na fashe da kuka na ba ta labari, amma ban ce mata planing na yi ba, sai ta rufe ni da faɗa ita wai laifina ma take gani, nunawa ta yi tun da har na shekara uku ban haihuwa ba to rashin adalci ne zai saka na hana mijina aure, kuma tun da ba wulaƙanta ni yake yi ba ai ya yi min da sauƙi, na kasa fahimtar da ita domin na ajiye wannan planing ɗin da na yi a matsayin sirri, haka ta ƙaraci nasiharta wacce take shiga ta fita daga kunnena, ɗaya ban ɗauka ba, tun da asirin ciki sai hanji, ni kaɗai na san wane ne Sadam. Kafin ta tafi sai da ta gyara gidan tsaf, ta yi girki mai yawa, ba ta tafi ba sai da na yi mata alƙawarin zan haƙura mu zauna lafiya da shi, amma da ta tafi na watsar. Kwana uku kenan muna 'yar ɓuya da shi, sai a na huɗun ne ya yi dadowar bazata, da azhar ya dawo, kuma ya bar motarsa a waje bai shigo da ita ba, don haka ban ankara ba ya ritsa ni a kitchen, ina yin meat pie, kawai sai shigowarsa na ji, duk na diririce, kuma na ɓata rai, ya tsaya yana kallona da idanunsa da suke burge ni a baya, amma wallahi yanzu Allah na tuba sai na ga idon kamar ma a shagiɗe, "Sayyada" Ya kira sunana a sanyaye. Na yi kamar ban ji ba, na zuba mai a kasko zan kunna gas din, ya shigo ya riƙe hannuna ya juyo da ni, ya ce"Kwana biyu ya gida?" Na fara ƙoƙarin fizgewa, bai ba ni dama ba ya ce"Ki yi haƙuri da abin da ya faru rannan, wallahi kin kai ni bango ne, ki dinga tunawa ni fa mijinki ne, wasu abubuwan da kike yi suna yawa". Na fara ƙoƙarin sakin hawaye, amma ina ta dagiya da su dai ba su zubo ba, ya ce"I miss You, mu je ki ba ni hakkina ko?" Na ce"Ai har abada! Tun da dai ka samu me ba ka, sai ka je ta ba ka, dama ai ba yau ta fara baka ba". Ya ce"Ba na son saka miki ƙarfi fa sai dole, Kodayake kin ce ma wai fyaɗe ne ko?" Ya ƙarasa da dariya. Ya ɗaga min gira ya ce"Mu je? Kin ga idan amarya ta zo za ki huta da ni". Na fizge na ce"Wallahi ba zan sake haɗa shimfida da kai ba, kuma ya zama dole ka sake ni". Ya yi tsaki ya ɗauke ni cak, ina ta dukan bayansa, da na ga dai ya kusa cim ma ɗakin nasa na fara faɗin"Ka ajiye ni, ni ka ajiye ne, ban yi tsarki ba fa, period nake". Ya ce"A tunaninki hidimar auren za ta saka na manta da kwanakin period ɗinki kenan". Ya dire ni a ɗakinsa, ya biya buƙatarsa, ya yi wanka ya fito ya ce"Tashi ki fita Malama zan rufe ɗakina". Kallonsa kawai nake ina hawaye na ƙi tashi, ya zo ya ɗauke ji da tarkacen kayan da ya cire min yana cewa "Na daina barinki a ɗakina, kar aljanunki su tashi ki kassara ni". Ya watsa ni kan doguwar kujera ya fice daga gidan. LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, DAGA YANZU ZUWA LOKACIN DA ZAN GAMA FREE PAGES ZA A SAKA 500 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay 08028966015 [30/09, 7:27 pm] Sadiya Abdulrazak: A yau dai na ji kamar tun da aka yi aurenmu Sadam bai taɓa tozarta ni irin haka ba, zuciyata ta dinga zafi, na daɗe kwance a hakan ina tunanin me na yi masa da na cancanci haka a gare shi? Ba na tuna komai sai sadaukarwa da na yi masa, da kuma tarin cutarwar da ya yi mini, ko da iya fushin da mahaifina yake yi da ni aka bar ni ai ya cuce ni, na rarrashi kaina na tashi, na yi wanka na saka kaya, na koma kitchen na ƙarasa abin da nake yi, na haɗa da lemo na ci meat pie ɗin, da na daidaici ya kusa dawowa gidan na ɗauko sauran daga kitchen ɗin na ɗauki yogurt na koma ɗakina na rufe, alƙawari na yi ba zai sake gani na ba, idan ya gaji ya ga babu amfanin zaman auren namu ƙila zai sake ni, aikuwa na yi ƙoƙarin kauce masa ɗin, bai gan ni ba, amma kullum sai ya zo ya leƙa ni ta window yana ta tambayata ina lafiya? Banza nake yi da shi, a wannan zaman ɗaki da nake yi addu'a kawai nake Allah Ya kawo min ƙarshen zaman ƙuncin nan, Sadam ya sake ni na huta, ba mu haɗu ba har sai ranar ɗaurin auren da safe, kwana na yi ina sallar dare, hakan ya sa na makara, sai ƙarfe bakwai na yi sallar asuba, kuma na tashi da yunwa, amma haka na daure ina jiran ya fita, tun da sai takwas da rabi yake fita, tun da lokaci ya yi nake baza kunne ban ji fitowarsa ba, sai na tuna ƙika ya fita tun sassafe tun da dai yau ake ɗaura aurensa, hakan ya sa na fito, daga ni sai wata guntuwar rigar bacci iya cinyata, ina fitowa na ji an fizgo ni, na firgita na ƙwalla ƙara, na yi mamakin ganin ko shiryawa bai yi ba, na fara fizgewa ina cewa "Sake ni, ka sake ni!". Ya ce"Haba Sayyada, wai ke sai yaushe za ki sassautawa kanki ne? Kishi hauka ne? Ba fa duka za ta kwace miki ni ba, sammata za ki yi, idan kika duba tsarin nan ke ce matar so, ita matar haihuwa ce da rainon 'ya'ya". Na ce"Kenan dai har yanzu ba ka fatan na haihu ko Sadam?" Ya ce"Wallahi ba haka ba ne, kawai dai ina nuna miki yadda nake sonki ne". Na ce"Cika ni don Allah". Ya ce"A'a taimakona za ki yi, ki ɗan rage min zafi, kin ga anjima ina gidan amarya, na san za ki yi kewata, sati ɗaya da yawa, shin za ki iya kwana ke kaɗai ma kuwa? Shi yasa na so na haɗa muku gida, amma gudun fitinarki na canza ra'ayi". Na ce"Sadam ba zan ma zauna a gidanka ba, ballantana na yi maka fitinar, in sha Allah zan bar maka gidanka, wallahi na tsane ka, ba zan sake son ka ba har abada". Na fizge na yi hanyar kitchen ɗin, ya ruƙo ni ya ce"Ki so ni ko kar ki so ni wannan zaɓinki ne, amma zama da ke ko rabuwa zaɓina ne, ban da ma ke shashasha ce na ga ni ne gatanki? Ke da ubanki ya sallama mini ke kamar baiwa, har mene ne abun sha'awa a ki kashe auren ki koma gidansa, Sayyada ko da na sake ki ki saka a ranki ke da jin daɗin zaman aure har abada, ni ɗin da kika tsana kika raina wallahi ni ne gatanki". "Tirr! Ai kuwa Allah wadai da wannan gatan, indai kai ne gatana wallahi ni ce shugabar asararru ta wannan zamanin, kuma mugun fatanka ya tabbata a kanka, In sha Allah za ka sake ni, kuma zan auri miji na gari, na yi rayuwar aure mai 'yanci, in sha Allah sai na rayu da wanda ya san darajata, mugu azzalumi, butulu". Ya ji zafin maganata ko a yanayin fuskarsa, ya yi murmushin gefen baki, sannan ya cije leɓensa ya jinjina kai ya ce"Shikenan, mu zuba mu gani, yanzu za ki ba ni hakkina ne ko kuwa sai na saka ƙarfin?" Cikin kuka na ce"Ka saka ƙarfin, don Allah kar ka bar ni har sai na ja numfashin ƙarshe, ka kashe ni don Allah". Na rushe da kuka Bai ji tausayin kukan nawa ba, ya tura ni kan kujera, ban yi wani yunƙurin hana shi ba kamar yadda na saba, haka ya yi yadda ya so da ni, ina ta kuka mai cin rai, ya gama ya yi tsaki yana cewa"Allah wadaran naka ya lalace, ban da ma dai amaryar ta tabbatar min a cikin period take me zan yi da ke a yau Sayyada?" Ban ce masa komai ba, ya koma ɗaki, na tashi ni ma na koma ɗakina, na fito daga wanka na zauna a bakin gado, zuciyata na zafi, ina ta tunanin matakin da ya kamata na ɗauka a kan Sadam, saboda har zuciyata na gaji da zaman auren nan, ina nan zaune ya shigo ɗakin cikin shirinsa na angwaye, ransa fess yana ta murmushi ya ce"To Sayyada, ni fa zan wuce, bayan ɗaurin auren zan shigo kafin na tafi ɗakin amarya". Na yi shiru ban ce komai ba. Ya ce"Kina buƙatar wani abu ne? 'Yan uwanki za su zo? To idan za ku yi girki ki faɗa min, kodayake bari na saka miki kuɗi sai ki yi abin da za ki yi, ni na tafi, so sorry Baby love". Ya tafi, na bi shi da kallo kamar sokuwa, yadda zuciyata ta yi rauni haka gangar jikina ma ta yi, ba ni da ƙarfin da zan dakatar da shi, na san ƙarshe dukana zai yi ma. Waya na ɗakko na kira lambar Anisa ba ta shiga ba, na kira Mama, muka gaisa, ta ce"Sayyada ya ƙarfin jikin naki? Kina lafiya ko?" Kamar ina jira na rushe da kuka sosai, ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Mene ne ya faru? Me ya yi miki?" Na ce"Yau ne! Mama yau ne, wallahi yau ne ɗaurin auren Sadam, ya tafi, ya tafi zai auro wata, Mama ko ku bar ni na dawo gida ko kuma na mutu, ba zan jure ba wallahi zuciyata ce za ta buga a yau ɗin nan". Na tsananta kukana sosai Mama ta ce"La haula wa la ƙuwwata illa billah! Haba Sayyada, ke kuwa wane kalar kishi ne da ke? Kishiya kanki farau? Waɗanda aka yi musu ɗin mutuwa suka yi? To wallahi ki kiyaye ni Sayyada, ko dai ki kwantar da hankalinki ki yi haƙuri, ko kuma ki ƙarasa ɓarar da garinki a wajen mijinki, domin yanzu yadda ya yi sabuwar amaryar nan babu abin da ba za ki gani ba". Na kashe wayar na ajiye, ina ji tana kira na ƙi ɗagawa, to me za ta ce min? Na gama lura babu wanda ya san yadda nake ji, ba za a fahimce ni ba, faɗin kukan da na sha a ranar ɓata baki ne, fuskata ta kumbura ta yi ja, ga shi Sadam bai dawo ba, babu wanda ya zo gidan a dangina ko ƙawaye, kodayake wa ba gayyata? Dama Anisa ce nake tunanin zuwanta, kuma ba ta zo ba, ta ma kashe wayarta, nan take na ayyana ƙila ma don ni ta kashe don kar ta zo, haka ba wuni cikin wani hali, amma hakan bai sa na ƙi jin yunwa ba wajen ƙarfe uku, ni dai na ga baƙincikin da zai sa na kasa cin abinci, shayi da biredi na sha tsaye a kitchen, na nemi waje na zauna a ƙasa dirshan, kawai gani nake duk duniya babu mai sona a yanzu sai Mama, ita kuma ba ta iya ja da maganar Baba, don haka ita ma ba ta da wani tasiri idan ba addu'a da take cewa tana yi mini ba, da na yi tsam na yi tunani sai na ga to idan haka ne mene ne amfanina? Ba ni da wani sauran amfani, idan na mutu ni kaɗai ce na yi asarar rayuwata, Sadam dai ba shi da asara tun da yana da wata matar a yanzu wacce ya ma fi so, iyayena suna da wasu 'ya'yan bayan ni, wanda nake da tabbacin yanzu sun fi son su fiye da ni, tun da su ba su saɓa musu ba suna yi musu biyayya, sannan ni ba ɗa ba ballantana jika, da na haihu shi ne nake da tabbacin yarana za su koka idan na mutu, tun da kuwa ba mai damuwa da mutuwata ai ya kamata a ce na mutu kawai, sauke idona da na yi a kan wuƙa ya yi daidai da tunawa da hukuncin wanda ya kashe kansa, kafin ma na mutu na tarar da wannan hukuncin ita kanta azabar da zan sha na tuna ta, tun da ban manta raɗaɗin da na ji ba lokacin da na yanka hannuna, ba zan kashe kaina ba, ba zan sake cutar da kaina a kan Sadam ba, don bai cancanci haka ba, sai dai na cutar da shi, 'Kashe shi zan yi?' Na yi wa kaina tambayar a zuciya, wata zuciyar ta ce'Mene ne ribarki idan kin kashe shi an kama ki kin ƙare rayuwarki a gidan yari?' A fili na furta "Babu! Shikenan kawai ya riga ya cuce ni". Gidanmu kawai zan tafi, ko kashe ni Baba zai yi sai dai ya yi, amma ba zan iya wannan zaman ba na takaici, na ɗauki waya na kira Mama, tana ɗauka na ce"Mama ki yafe min, don Allah ki cewa Baba ya yafe min". Mama ta ce"Sayyada ai mun yafe miki, me kuma ya faru?" Na ce"Gani nan a kitchen riƙe da wuƙa zan kashe kaina na huta, tun da babu mai sona babu wanda ya damu da rayuwata, Mama zan kashe kaina fatana kawai ku yafe ni". A matuƙar ruɗe Mama ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi! Sayyada! Kar ki yi, kar ki sake ki aikata wannan babban kuskuren, don Allah kar ki cutar da kanki, ki kamo hanya ki taho gida, Babanki zai karɓe ki, ki tuna rainon ciki da zafin haihuwa, ki tuna shayarwa da rainonki da na yi har zuwa girma, ina son ki har gobe, har abada, idan kika illata kanki ba ki yi mini adalci ba, kuma sai Allah Ya yi mana hisabi da ke" Ta fara kukan da ya tashi hankalina. Ni ma cikin kukan na ce"Shikenan Mama, na fasa, ki daina kuka, zan haƙura na zauna har ciwon zuciya ko na damuwa ya yi ajalina, zan zauna da Sadam baƙincikinsa ya kashe ni Mama..." Na rushe da kuka. Ita ma kukan take yi ta ce"Sayyada ki taho gida na ce, ki haɗa kayanki ki taho gida". Na ce"Ba na son abin da zai ja miki matsala da Baba, Mama ba na so..." Ta daka min tsawa ta ce"Na ce ki taho gida!" Da sauri na ce"To, gani nan". Na hau haɗa kayana a babbar jaka, na tattara komai nawa me amfani na saka hijjabi na bar gidan, mai gadi bai hana ni ba, tun da ba a ba shi wannan umarnin ba, ina zuwa ƙofar gida na tarar da Baba yana alwalar sallar la'asar, gabana ya fara faɗuwa, haka na daure na tunkare shi, ina hawaye, na duƙa na gaishe shi murya a dashe, ya bi ni da mugun kallo kafin ya ce"Ina za ki je da wannan uwar jaka?" Na ce"Gida na dawo Baba, na gaji da auren nan, don Allah ku yafe ni, na tuba, wallahi na gane kuskurena". Baba ya ce"Maza ki koma inda kika fito, wallahi ko sakinki ya yi na faɗa miki ba ki da matsuguni a gidana, ni da ke har abada! Sayyada cutarwar da kika yi min ki sani sai Allah Ya yi mini hisabi da ke, ki koma inda kika fito, kuma idan kika je gidan wani ɗan'uwana ban yafe miki ba!". Ya tafi masallaci ya bar shi tsaye ina kuka, ga masu wucewa zuwa masallaci sai kallona suke yi, ban ji maganarsa ba, haka na ja ƙafa na shiga gidan ina ƙara sautin kukana, Mama ta zo ta rungume ni tana kukan ita ma, ta ce"Sayyada duk na jiyo tattaunawarku, ba ki da wajen zuwa da ya wuce nan gidan, so yake ki shiga duniya ko kuma zama za ki yi ɗan iskan mijinki ya kashe ki?" Ta tura ni a ɗakinmu na yara, ina kuka, ta zaunar da ni, tana cewa"Idan har ya hana ki zama to ni ma ba zan zauna ba, sai dai mu tafi tare, me yasa maza ba su san ciwon mace ba? Ai ni dama na sani, mijinki ba zai taɓa daraja ki ba, saboda kin cuci kanki ki ɓarar da darajarki a idonsa". Zuciyata ta cika da fargabar hukuncin da Mama take son yankewa, na ce"Mama don Allah kar ki yi haka, kar ki bari Baba ya yi fushi da ke, tun da kuka haife ni na taso ban taɓa ganin kun samu saɓani ba sai ta silata, idan aurenki ya mutu ta dalilina wallahi na cika asararriya, ba zan yafewa kaina ba, rayuwata ma ba za ta yi albarka ba, zan tafi Mama ki yi min addu'ar fatan alkhairi, na yi miki alƙawarin ba zan taɓa sake aikata kuskuren da na aikata a baya ba, zan tsare mutuncina a duk inda nake". Mama ta ce"Me da me yake yi miki ne? Abun ya yi tsananin da ba za ki iya haƙuri ba?" Na ce"Komai ma yi min yake ma, abubuwan ba za su faɗu ba". Ta ce"Ki zauna, ko yaya ne ki ba shi iska, zan faɗawa Babanki ba ki shigo ba, sai ki bari sai ya fita sannan za ki dinga fitowa tsakar gida". Na gyaɗa mata kai alamar na amince. Ta tashi ta bar ɗakin. Baba yana dawowa daga masallaci ya fara faɗa yana tambayar ina nake? Da sauri na ja jakata na laɓe a bayan ƙofa, ina ji Mama tana ce masa ban shigo ba, ya cigaba da sababi yana cewa ko gidan wani nashi bai amince na je ba, gawata kawai zai gani ya yafe min abin da na yi masa, na guntse baki ina sakin kuka, yanzu idan ya riga ni mutuwa fa? Hakan na nufin ya tafi bai yafe min ba? Wace irin zuciya ce da Baba? Da daddare Mama ta kawo min abinci na ci, ta zauna tana ta kwantar min da hankali. A haka na yi sati ɗaya cir a gidanmu, ba na taɓa fitowa sai Baba ba ya gidan, na yi mamakin yadda Saddam bai kira ni ba, na sake tabbatarwa ba ni da wani sauran mutunci a idonsa, wato ya samu amarya har ya manta da ni, hankalina har ya fara kwanciya, saboda da gaske fa ba na son ganin Sadam ballantana aurensa. Ashe shi duk bai san wainar da ake toyawa ba, yana sane ya ƙi kirana, ya ƙi zuwa gidana, saboda ya hukunta ni da hakan, bai taɓa zaton ba na gidan ba, sai da ya gama sati ɗayansa da amarya cikin kwanciyar hankali, a ranar da ya dawo gidana ya ga ba na nan, mai gadi yake faɗa masa ai tun ranar aure da na fita ban dawo ba, hankalinsa ya tashi. A ranar ina kwance ina bacci da safe ina jiyo firar Mama da Baba a tsakar gida sai ga kiran Sadam ya shigo wayata, da yake a silen take ban sani ba, sai da ya yi kira uku, a na huɗun ne na ga waya tana haske, ina ganin sunan shi gabana ya faɗi, na kashe wayar bakiɗaya, babu jimawa kuma na ji sallar yaro, tare da faɗin"Wai Sadam yana sallama da Sayyada". Ƙirjina ya doka da ƙarfi, har sai da na dafe shi, Baba ya ce"Ka je ka ce babu Sayyada a gidan nan". Yaron ya dawo ya ce"Wai ya ce mijinta ne, yau sati ɗaya ba ta gidansa". Mama tuni gumi ya fara yanko mata, ta ɗauki buta ta shige banɗaki, Baba kuma gabansa ya faɗi ya yi tsam da jin ashe ban koma gidana ba, amma ya maze ya ce"Ka ce masa ba ta zo nan ba". Ina ɗaki a tsaye a bayan ƙofa ina ta gumi sai jin sallamar Sadam na yi ya shigo cikin gidan, na ƙara ruɗewa, ya gaishe da Baba ya amsa a taƙaice, Saddam ya ce"Baba dama Sayyada ce..." Baba ya katse shi da faɗin"Ba na son jin komai! Ta zo nan amma ko gidan ba ta shiga ba ta koma, don haka sai ka san inda za ka tafi nemanta". Saddam ya ce"Don Allah Baba ka yi haƙuri, na san tana gidan nan, kawai dai ranku ne ya ɓaci, ba za ta je ko'ina ba ban da nan, don Allah a yi haƙuri, zan gyara idan laifi na yi mata". Baba ya ce"To ban san kuma da wane yaren zan yi maka magana ka fahimta ba, yanzu ni na yi maka kama da wanda zan yi maka ƙarya kenan? To kai ma ka sani, ko sakinta ka yi ba ta da wajen zama a gidana, ballantana kuma yaji, don haka ka tashi ka bar min gida". Sadam ya shiga ɗaga hanci yana shaƙo numfashi kamar sabon maye, ya ce"Amma Baba kamar fa ina jin ƙamshinta, ina nufin turarenra". Ya tashi tsaye, ai kuwa ya ga ashe a kusa da hijjabinta dake kan igiya ya tsugunna, ya gane hijjabin kuma ya tabbatar da ƙamshin, ya ce"Wallahi Baba Sayyada tana cikin gidan na , don Allah ku fito min da matata mu tafi, Wallahi zan gyara, wasu abubuwan kuma laifinta ne". Baba ya rasa abun cewa, can kuma sai ya tashi ya leƙa ɗakin Mama, ya dawo ya leƙa ɗakin da nake, ina bayan ƙofa ni da kayana, amma wayata tana yashe a tsakar ɗakin, ya ƙarasa cikin ɗakin ya ɗauki wayar da Sadam ya kira ko zai jiyo ringing a cikin gidan, ya ce"Wannan wayar..." Ido huɗu da muka yi ya sa ya ƙarasa maganar, na fashe da kuka ina cewa "Baba ka yafe min". IN SHA ALLAH GOBE ZAN KAMMALA FREE PAGES, GOBE BA ZAN KARƁI 500 BA, DISCOUNT ZAI ƘARE A YAU, 700 NE LABARIN NAN 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay 08028966015 [01/10, 5:41 pm] Sadiya Abdulrazak: Da matuƙar mamaki mai haɗe da tsantsar ɓacin rai ya ce"Sayyada!?" Na maƙale a jikin bangon ina maƙerƙeta, saboda na yi zaton dukana zai yi, amma sai na ga ya fita yana ƙwalawa Mama kira, ta fito daga banɗakin da ta ɓuya ita ma tana karkarwa ta ce"Na gaji, na gaji da yadda rayuwar 'yata take ƙunsar takaicin namiji me yasa maza ba kwa yi mana adalci ne?" A fusace Baba ya ce"Au haka kika ce? Ni ne mara adalcin? To ki tattara 'yar taki ku bar min gida, wallahi sai kun bar gidan nan, idan Sayyada ta sake kwana a gidan nan a bakin aurenki!". Na fito da sauri ina kuka na duƙa a gaban Baba na kama ƙafarsa zan fara yi masa magiya, ya yi min wata ƙafa sai da na gangara, Sadam ya taho da sauri ya tada ni tsaye ya rungume a ƙirjinsa yana cewa"Baba don Allah ka yi haƙuri". Na fara ƙoƙarin janyewa daga jikinsa ina cewa"Ka rabu da ni, ya dake ni ɗin indai zai wuce, don Allah Baba ka kashe ni idan na zama gawa na san na zama free za ka yafe min". Mama ma kukan take ta ce"Na yarda zan bar maka gidanka, gara na haƙura da auren na zauna da 'yata na jiɓanci lamarinta, Allah ma muna yi masa laifi ya yafe mana ballantana kai ɗan'adam". Na ce"Don Allah Mama kar ki yi haka, ni ban cancanci ki ɓata aurenki saboda ni ba, zan tafi kawai amma wallahi ba zan cigaba da rayuwa a gidan Sadam ba, idan kuma aka matsa min komai zai iya faruwa" Na fashe da kuka sosai. Sadam ma idonsa ya yi ja, ya ce"Baba Sayyada fa 'yarka ce, a duniya na tsani na ga wani yana tozarta ta tun ranar da na aure ta, ko ba ka kore ta ba dama wallahi ba zan bari ta zauna ba, ai ba sakinta na yi ba, kuma ba zan sake ta ba, ko mutuwa na yi yau na bar wasiyya kar Sayyada ta dawo gidan nan, ta zauna a gidana na mallaka mata shi halak malak daga yau, ke ki wuce mu tafi!" Ya ƙarasa da daka min tsawa rai a ɓace. Sam bai burge ni ba, haushi ya ba ni soyayya, domin wannan abin da Baba yake yi min bai saka na ji ba na son shi ba, abu ɗaya na sani na yi masa babban laifi shiyasa ya kasa yafe min, na ce"Kar ka sake ka ce za ka faɗawa mahaifina magana, kuma aurenka na ce na gama shi, don haka dole ka sake ni". Ya ce"Ina kayan naki suke?" Bai jira amsata ba ya shiga ɗakin ya ɗakko jakar. Ya kalli Baba ya ce"Ba dai ba ka son ganinta ba? In sha Allah ba za ka sake ganinta ba daga yau". Sannan ya kalli Mama ya ce"Mama ki yi haƙuri ki zauna ki riƙe aurenki, ko kin kashe aurenki ba za ki rayu da Sayyada ba, don wallahi babu kotun da ta isa ta saka na sake ta ballantana mutum, amma ki saka a ranki 'yarki tana cikin aminci, idan ta shiga ƙunci ita ta so". Ya kalle ni ya ce"Sayyada mene ne amfanin zama a inda ganinki a wajen zai haddasa husuma da ɓace-ɓacen rayuka? Na yi miki alƙawarin kyautatawa daga yau, wallahi zan zauna da ke bisa adalci idan a baya ina yi miki abubuwan rashin adalci yanzu zan gyara zan yi miki adalci". Ya riƙe hannuna yana cewa"Mu je gida, mijinki yana tare da ke har ƙarshen numfashinsa". Na firge, ya sake damƙar hannuna ya fizge ni zuwa waje, ya jefa ni a motar ina ta kuka ya ja muka tafi, ban tsagaita da kukan ba shi ma bai rarrashe ni ba har sai da muka ƙarasa gida, ya faka motar ya ce"Ki fito". Na ce"Wallahi Sadam cigaba da rayuwa tare da ni ba zai yi maka daɗi ba, za ka yi danasanin dawo da ni gidan nan". Ya ce"Na ji na yarda, indai ke zai yi miki daɗi ai shikenan". Na ce"Na tsane ka Saddam, ka kiyayi zama da wanda ya tsane ka musamman ma mace". Ya yi shiru yana kallona, ni ma shirun na yi ina jin yadda tsanarsa ke ta'azzara a zuciyata wallahi ji nake shi ne wanda na fi tsana a duniya, sai yanzu nake ganin girman cutar da ya yi min, ina zan kai fushin mahaifina? Ya ce"Sayyada, ki yi haƙuri kin ji? Amma idan kika duba ba ki da wata mafita wacce ta fi mu cigaba da rayuwar aurenmu, in sha Allah za ki samu haihuwa idan ma don ita ce, kuka kishiya babu ruwanki da ita, wallahi ba zan rage komai da nake yi miki na kulawa ba a matsayinki na matata, ni fa ba mahaukaci ba ne, ba kuma ba ni da zuciya ba ne, wannan ƙiyayyar da kike nuna min da rashin kunya abun yana yi mini zafi sosai, kawai ina daurewa ne saboda na san a baya na cutar da ke, sai nake ganin na dawwama da ke na riƙe aurenki da amana shi ne zai wanke ni a zuciyarki da kuma idon iyayenki, amma kin ƙi ba ni haɗin kai, ya zan yi ne? Me kike so na yi miki ki yarda da ni?" Na ce"Ka sake ni, sakina kawai za ka yi na yarda kana sona kuma ka yi min halakci, don Allah idan kai ɗan halak ne ka sake ni Sadam". Ya yi huci mai zafi, ya fita daga motar, ya zagayo inda nake ya fito da ni, cak ya ɗauke ni ya dire ni a falo, ya ce"Kina jin yunwa ne?" Na yi banza da shi ina ta kuka. Ya zauna ya riƙe hannuna yana ta wasa da shi, ya ce"Sayyada". Ban amsa ba, ya cigaba da faɗin"Don Allah ki dakata da wannan shirmen, ina sonki, kina sona..." Na katse shi da faɗin"Gyara kalamanka, ka ce dai a da na so ka, amma wallahi ban da yanzu". Ya ce"Yanzun ma kina sona, ɓacin rai ne kawai, kuma na san za ki huce, yanzu dai ina so zamanmu ya dawo kamar farko, mu rayu cikin farinciki don Allah". Na daka tsaki na ce"Ko za ka kwana ka wuni kana magana abu ɗaya kawai nake jin kana maimaitawa, kalmar saki kawai za ka furta min na san an samu cigaba a kalamanka". Ya ce"Ai kuwa ba za a samu cigaban ba, ni dai Allah Ya sani na yi iya yina, tun da taurin kai ne da ke ki je ki yi duk yadda kika ga dama, amma kar ki manta ni mijinki ne, aljannarki tana ƙarƙashin ƙafata". Na ce"Ai ba miji irinka ake nufi ba". Ya ce"Ok, ko me za ki yi, ki yi, ga wajen nan". Yana gidan a ɗakinsa ni ina falo ina ta ƙunar zuciya, har aka kira sallar azhar, ya fita masallaci, na tashi na ɗauki jakata na fito ba don na san inda zan je ba, amma kawai burina na yi nesa da shi, na gujewa aurensa, na ji daɗin ganin Baba mai gadi ba ya nan, da sauri na ƙarasa, sai dai ina zuwa na ga kwaɗo a jikin ƙofar, na san dai ni ake tsarewa, tun da don zai tafi sallah ba ya rufe ƙofar ta ciki, na ja jiki na koma ina hawaye, ni ma sallar na yi, na zauna ina ta tunanin mafita, wata zuciyar ta ce na haƙura na zauna da Sadam mu gyara zaman, wata kuma ta ce idan ban bar gidansa ba baƙincikinsa ne zai kashe ni, saboda duk daɗin baki yake yi mini ba zai canza hali ba, kuma na fi yarda da ba zai canza ba ɗin, tun da tun yaushe muke tare? Tun yaushe yake cuta ta? Bai dawo da wuri ba, saboda sai da ya je ya siyo mana abinci, ya shigo fuskarsa babu yabo babu fallasa ya ajiye min, na shige ɗakinsa da na shi, wajen la'asar ya fice daga gidan bai kula ni ba, bayan magriba ya dawo da abinci a kula, ya ajiye min, nan take na fara tunanin daga gidan shegiyar matarsa ya karɓo, don haka na ce"Ka ɗauke ba zan ci ba". Ya ce"Ok". Ya matsar da shi daga gabana, ya ce"Sayyada, yau na dawo ɗakinki, kuma kwana biyu za a dinga rabon kwanan, ai ya yi ko?" Takaici ne ya hana ni cewa komai, ina raba shi da kiwon kyalle yana kyalle ta haihu? Ya ce"Sayyada". Ban amsa ba, ban ma kalle shi ba, ya ce"In sha Allah daga yanzu ba zan sake takura miki ba, amma ba zan sake ki ba, sai dai kuma ba za ki sake fita daga cikin gidan nan ba har sai na gamsu da yadda kika karɓi zaman aurenmu, komai kike so ki faɗa min zan kawo miki, sabga kuma idan ta tashi ki dinga Allah Ya sanya alkhairi a waya, ba zan gajiya wajen yi miki addu'ar nema miki shiriyar Allah ba, sannan zan fara yi miki ta gujewa fushin Allah, ni mijinki na yafe miki". Daga haka ya tashi ya fita daga gidan, ina nan zaune a falon ya dawo can bayan sallar isha'i, ya wuce ni yana waya ya shiga ɗakinsa ya rufe, har sha ɗaya ina nan a zaune, bacci da yunwa sun addabe ni, haka dai na buɗe kular na ga faten doya ne da kifi, na tashi na je kitchen na ɗakko faranti na zuba na ci, ni ce har da ƙari, kamar na manta daga hannun kishiya ya fito, na shiga ɗakina na yi wanka na canza kaya ka kwanta, nan take bacci ya yi gaba da ni. Washegari ya dafa shayi ya karya, ya yi tafiyarsa aiki, ni ma guntun shayi da biredin na ci, wajen sha biyu ya aiko da cefane mai yawa, a raina na ayyana wato dai shi ya dage ni da shi zama daram ko? Na yi girki iya cikina, na ci, na kai wanda zan ci da daddare ɗakina, na wanke komai kamar ban yi ba, don ba na so ya san na yi ɗin, so nake ya gane da gaske ba na zaman auren nan, ko zai sake ni na huta. Bai dawo ba sai bayan sallar isha'i, ina ɗakina ya turo ya shigo, ya ce"Sayyada na ki yi girki ba ne?" Na ce"Ban yi ba, ai ni da girki a gidan na. Har abada!". Ya ce"To Allah Ya raba ki da cutar yunwa". Ya fita, ina jin sanda ya fice da mota daga gidan, ya dawo ya shigo ya ajiye min takeaway na ƙi kula shi, a nan ya zauna ya ci na shi, ya sha ruwa, sai na ga yana rage kayan jikinsa, ya gama ya hau gadon, da sauri na tashi zaune ina cewa"Ka fitar min daga ɗaki". Ya ce"Ba zan samu hakkina ba? Gobe fa zan bar gidanki, wai kar na barki da kewata". Na ce"Allah Ya kiyaye, wacce ta damu da kai ita ce za ta yi kewarka, har abada ba zan sake baka haɗin kai, sai dai idan fyaɗen da ka saba za ka yi". Ya sauka gadon ya ce"Ai na daina yi miki har abada, sai da safe". Ya fice daga ɗakin. Washegari duk da yana ɗakin Safna sai da ya zo gidana da safe, ganina kawai ya yi bai ce komai ba ya tafi, washegari ma haka. Ranar dawo ɗakina ma haka ba ya shiga harkata, kuma ranar da zai bar ɗakina ya sake zuwa ya ce zan ba shi hakkinsa? Na ce a'a, sai ya ce Shikenan duk ranar da na ji ina bukatarsa na sanar da shi, shi dai ba zai sake nema na ba, daga ranar kuwa bai sake nema na ba, har tsawon wata ɗaya haka muke zaman kowa ya yi ta kansa, ya riga ya saba ba na ba shi abinci, iya cikina nake girkawa. Wata ranar Lahadi da ba zan taɓa mantawa da ita ba, ranar ba ma ni ce da kwana ba, a gidan Safna yake, ina ta bacci wajen sha biyu, na ji shigowar mutum ɗakina, ya kunna hasken ɗakin, Sadam ne tsaye daga shi sai ɗan wando, ya yi min murmushi, na ɓata rai, ya ƙaraso ya zauna a bakin gadon ya ce"Yau fa Safna ba ta nan, aikin kwana take yi, kuma dama tana period, ni kuma na kasa jurewa, shi ne ta ce ta amince na zo gare ki". A harzuƙe na ce"Ni ban amince ba, kenan ma ba ka faɗa mata na bar mata kai ba har abada?" Ya ce"Don Allah Sayyada mene ne matsalarki? Kin san fa ba daidai kike aikatawa ba, ya kamata a ce zuwa yanzu mun wuce wajen". Na yi banza da shi. Ya ce"To ya za ki yi da ni yanzu? Za ki ba ni ne?" Na ce"Ka ƙwata mana! Ko dama da ka ce ka daina yi min fyaɗe kana zaton na yarda ne?" Ya ce"Yanzu idan za a ba ki zaɓi za ki zaɓi na je wata a titi ta ba ni?" Na ce"Ai dama ka saba!" Ya ce"Na yafe miki duka ƙazafin da kike yi min". Ya janyo ni jikinsa, duk duka da yaƙushin da nake yi masa bai rabu da ni ba, sai da ya cim ma muradinsa, zuciyata ta dinga zafi, ya shiga ya yi wanka a banɗakina, ya kwanta bacci ya kwashe shi. Na tashi zaune ina fashewa da kuka, kallonsa da nake yi ne ya dinga ta'azzara ƙiyayyarsa a zuciyata, shikenan haka zan cigaba da rayuwa cikin rashin 'yanci? Sam ban san inda na dosa ba fa, ba zai yiwu ba, Saddam ya yi kaɗan na kashe rayuwata saboda shi. Ina wanka ina kuka, na gama na saka doguwar rigar atamfa, na haɗa kaya a jaka, na fice daga ɗakin, ga mamakina ƙofar dai a kulle take ta ciki, na shiga ƙwanƙwasawa mai gadi, ya buɗe ya fito daga ɗakin nasa, na durƙushe a ƙasa ina kuka na ce"Baba indai kai uba ne ka yi tunanin yadda za ka ji idan 'yarka ta kasance a halin da nake ciki, don girman Allah ka buɗe min ƙofar nan na tafi gidanmu don Allah". Baba ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Ki yi haƙuri 'yata, komai ya yi zafi maganinsa Allah, ki yi ta faɗawa Allah, idan yana cutarki shi zai yi miki kyakkyawar sakayya, ba zan iya buɗe miki ƙofar nan ba, amma na lura kina cikin tsanani, yanzu dare ne, gobe da safe na yi miki alƙawarin zan buɗe miki ki tafi 'yata". Na ce"Don Allah Baba ka buɗe min yanzu, zan iya mutuwa idan na kwana a gidan nan". Ya ce"Ki yi haƙuri, yadda ba zan iya bari 'yar da na haifa ta fita daga gidan cikin daren nan ba, haka ke ma ba zan bar ki ba, da yau da gobe duk ɗaya ne, awa ne ma ya rage mu ga wayewar garin? Ki yi haƙuri kin ji? Ki je ki ɗaura alwala ki yi sallah, Allah zai kawo miki sassauci". Na gyaɗa masa kai, na ja jakar kayana na koma ciki, amma sai dai kash, ƙaddara ta riga fata, inda na yarda na ɗauki shawarar Baba mai gadi ƙila da abubuwa da yawa ba su faru ba cikin rayuwata, cikin ɗakin na koma na zauna a falo na fashe da kuka sosai, zuciya ta dinga yi mini ayyane-ayyane, a haka ne ta ayyana min me zai hana na kashe Sadam? Ai dai ba wanda zai min tilas ɗin zama da gawa ko? Ba tare da tsayawa tantance shawarar zuciyata ba, na yi kitchen na ɗakko wuƙa na tafi ɗakin nawa. Yana kwance ya baje sai sharar bacci yake yi hankali kwance, na tsaya ina kallon shi da wuƙar riƙe a hannuna, wallahi na kasa tuna kyautatawa ko guda ɗaya da ya yi min, sai tarin ƙuntatawa da cutarwa ne suke ta zuwa kaina, zuciyata tana ta faɗa min shi ne matsalata, kuma ina da maganin matsalar, na kashe shi kawai na huta. Duk taku ɗaya da nake yi na matsawa kusa da shi, ƙara bugun zuciyata ake yi, gabana sai faɗuwa yake, haka har ya zamana na matsa dab da shi, babu wani sauran taku, na ɗaga wuƙar cike da zugar zuciya da ta shaiɗan, sai dai na kasa daɓa masa ita a ciki kamar yadda na san zan fi kashe shi cikin sauƙi, sai kuma na sauke, sai da na ɗaga wuƙar sau biyu ina fasawa, a na uku da na ɗaga na daddage na caka masa a santaleliyar cinyarsa, na finciko ta da sauri, ya zabura ya saki wani gigitaccen ƙara sannan ya fara salati, tuni jini ya fara malala a gadon, na sake ɗagawa kamar zan caka masa na ce"Sadam za ka sake ni ko sai na kashe ka?" Zare ido yake cikin azabar ciwo da mamaki, ya ce"Sayyada? Kashe ni za ki yi?" Na ce"Za ka sake ni ko na ƙarasa ka?" Yana fizgar numfashi ya ce"Na...na...na sake ki, Na sake ki Sayyada". Ya fara kwarara ihu yana riƙe ƙafar. Jikina ya hau rawa, na fita da gudu ina ƙwalla kiran mai gadi, "Baba! Baba ka zo ka taimake ni, zai mutu". Ya fito da sauri, ya yi cikin gidan ni kuwa cikin farincin yau gidan a buɗe yake na buɗe na fice da gudu, ina ta haki, na yi nisa da gidan rigata ta harɗe ni na faɗi, daidai lokacin kuma na ji marata ta murɗa, na saki kukan azaba da nadama, da ƙyar na tashi ina jin ruwa mai yauƙi yana bin ƙafata amma ban fasa sauri ba, don na kasa yin gudu. Yau dai Sadam ya sake ni, amma tun a ranar na kasa jin farincikin da na yi tsammani, a tunanina rabuwa da Sadam ita ce hanyar buɗe shafin farincikina, ashe shafin ƙunci ne zai buɗe min, ku biyo ni don jin yadda rayuwata ta kasance. LAST FREE PAGES! DAGA WANNAN SHAFIN FREE PAGES SUN ƘARE, LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN 700, IDAN YA ZAMA COMPLETE 1K NE 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay 08028966015 [04/10, 8:26 am] Sadiya Abdulrazak: 12 Na yi tafiya mai nisa, na ji ciwon ya turnuƙe ni, na nemi waje gefen titi na zauna ina riƙe marata ina ta kuka, kalmar Na sake ki Sayyada ce take amsa kuwwa a kunnena, na fashe da kuka sosai ina cewa"Allah na tuba, ba ni da wani zaɓi ne da ya wuce wannan, Allah ka sani wannan bawa naka Sadam ya fi tsohon maye naci, Allah ka yafe min". Ina nan zaune a wajen cikin wani hali, sai ga 'yan bijilanti suna zagaye, suka haske ni da fitila, na kare fuskata ina cigaba da kuka. Suka ƙaraso suna tambayata wace ce ni kuma me ya fito da ni titi da daddare? Na ce musu mijina ba ya gari, kuma ni kaɗai ce a gidan na ji ina ciwon mara shiyasa na fito, suka tambaye ni ina ne gidan nawa na kwatanta musu a tsorace, suka tambayi lambar mijin, sai na saka tsohuwar lambata da na daɗe da canzawa, don haka da suka kira ba ta shiga ba, da na ga dai za su tsananta bincike na fasa musu kuka, na ce su kai ni gidan iyayena ba asibiti ba, don kuwa can na dosa. Ɗaya daga cikinsu ya ce"Asibiti kika fi buƙata, na ga kina zubar da jini". Sai a lokacin na kalli bayana, na ga yadda rigata ta ɓaci, gabana ya faɗi, amma duk a zatona tashin hankalin da na shiga ne ya matso da al'adata ta zo kafin lokacinta, sai dai ciwon marar ya tsananta, ko zan yi al'ada ba na irin ciwon nan mai tsanani, na ce"Ni dai mu je gidan namu, daga can ma je asibitin". Wani cikinsu ne ya je ya ɗakko adaidaitasahu muka shiga, ina yi musu kwartance har muka ƙarasa gidan, hankalina a tashe sai karkarwa nake, ina tunanin ya mai gadi ya ƙare da Sadam? Tun da ba lallai ya iya tuƙin mota ba, kar fa ya mutu, idan ya mutu ta tabbata na yi kisan kai kenan. Ƙwanƙwasa ƙofar gidanmu suka shiga yi, an ɗan daɗe ana bugun kafin Baba ya fito bai buɗe ba ya tambaya wane ne, cikin kuka na ce"Baba ni ce, Sayyada ce". Baba ya ce"Sayyada? Ke wane irin kunnen ƙashi ne da ke wai? Sau nawa zan faɗa miki na tsame ki daga cikin 'ya'yana? Wallahi Sayyada ki kiyayi ranar da zan sheme ki!". Na koma da baya na sakin sabon kuka, ɗaya daga cikinsu ya ce"Baba ya kamata ka buɗe, mu ma'aikata ne, mun tsince ta ne a titi, ko ma mene ne a tsakaninku bai kamata ka ƙi fitowa, ya kamata ka saurare mu". Baba bai buɗe ba ya ce"Wannan yarinyar a da ne take 'yata, amma yanzu ba 'yata ba ce, ko mene ne ya same ta Kar a sake nema na". Na fashe da kuka na ce"Don Allah Baba ka yi haƙuri, kuma ma Sadam ɗin ya sake ni, ina zan je da ya wuce nan ɗin?" Wallahi shiru ba a ƙara jin motsin Baba ba, da alama ya koma ya kwanta. Suka kalle ni duka da neman ƙarin bayani, na ce"Don Allah kar ku ce komai, ku rabu da ni a nan ɗin, kawai zan kwana a nan, gobe sai na sake roƙonsa". Fir! Suka ƙi, suka ce ba za su bar ni cikin haɗari ba, ƙarshe sai na ce mu je gidan yayansa wato baban su Anisa, duk da ban manta ba Baba ya ce idan ba sake zuwa gidan wani ɗan'uwansa bai yafe min ba, amma ba ni da wani zaɓi wanda ya wuce na je can ɗin. Shi ma dai bai buɗe ba sai da na yi bayanin ni ce, ya buɗe suka yi masa ƙarin bayani, cikin kuka na ce"Baba don Allah ka taimake ni ka ba ni wajen zama, ban san inda za ni". Baba ya fara salati ya ce"Sayyada, sai yaushe wannan abubuwan za su ƙare ne?" Na kasa cewa komai, suka yi masa bayanin asibiti ya kamata a fara kai ni, da maman Anisa muka tafi asibitin, kafin mu ƙarasa ma har mai afkuwa ta afku, domin kuwa muna zuwa asibitin aka tabbatar mana da ɓarin ciki na yi, gabana ya faɗi da ƙarfi, har hawa da saukar numfashina ya canza, na ce"Da gaske ciki ne da ni? Ina da ciki? Don likita ki ce min bai zube ba". Ta ce"Ki yi haƙuri, Allah zai ba ki wani in sha Allah, da alama ƙarami ne, shi yasa ba a sha wuya wajen fitar ta shi ba, ki lissafa ki gani yaushe rabonki da al'ada". Na yi tsam ina hawaye ina tunani, a lissafina sati biyar kenan ban yi al'ada ba, kuma ina zargin a wannan fyaɗen da Saddam ya yi min ya kwashe ni ya zubar a falo na samu cikin nan, na runtse ido ina jin kamar kaina zai yi bindiga, wata nadama ta rufto mini, wallahi inda na san ina da ciki da na bi komai a sannu, idan ban manta ba yau Sadam da ya zo ce mini ya yi matarsa tana period ba zai iya jurewa ba, kenan da burina zai cika zan riga ta haihuwa ma, ashe na yi gajen haƙuri,, tsakani na da Allah har da zafin rashin haihuwa da kuma tunanin wata za ta riga ni haihuwa ya sa na aikata wannan abun, da na san ina da ciki da na rabu da Sadam ya je can ya ƙarata da matarsa, yanzu ma ko a wane hali yake? SADAM Azabar da yake ji a ƙafarsa bai sa mamakin Sayyada kashe shi ba, bai taɓa zaton ƙiyayyar da take yi masa ta kai haka ba, tun da ta iya saka wuƙa ta yanka kanta ya san don ta caka masa a cinya ba komai ba ne, amma dalilin da ya sa ta caka masa ɗin ne ya ba shi mamaki, a wannan zamanin da mata suke neman mijin aure ido rufe? Me ta rasa mene ne ba ya yi mata? Mai gadi ya shigo da sauri yana bin inda yake jiyo kukan shi, ya same shi cikin jini ya fara salati yana cewa"Yanzu ya za a yi? Bari na samo mai adaidaitasahu". Sadam ya girgiza masa kai ya ce"Je ka bugawa maƙocinmu sai ya kai ni a mota, bari na kira shi". Da ƙyar ya nemi lambarsa ya faɗa masa, ya kuwa fito da mota da sauri, suka saka shi a ciki suka tafi asibiti, suna ta tambayarsa abin da ya faru, ya ƙi cewa komai, da suka je asibiti ma aka tambaya sai ya ce dare ya yi masu ƙwacen waya suka tare shi a hanya, shi dai mai gadi bai yarda ba, tun da yana kyautata zaton ba haka aka yi ba, aka shiga ba shi taimakon gaggawa. Allah dai ya taimaka wuƙar ba ta tsinka wata jijiyar ba, don haka matsalar ba mai yawa ba ce, duk yadda Sadam ya so ya ɓoye Sayyada ce ta yi masa wannan abun sai da aka gane ita ce, don da Abbansa ya ritsa mai gadi ya sanar masa lafiya lau ya shiga gidan, kuma sannan Sayyada ce ta zo ta faɗa masa halin da ake ciki, kafin nan kuma dama ta ce ya buɗe mata ta fita ta ƙi, don haka ita yake zargi, tun da ba ta jira aka kai shi asibiti ba ma ta gudu daga gidan. Shi Sadam bai san me ake ciki ba, sai ji ya yi Momynsa ta zo tana faɗa tana cewa sai ta ɗaure Sayyada har danginta, gabansa ya faɗi ya ce"Momy mene ne ya faru?" Ta daka masa harara ta ce"Au tambaya ma kake yi? Ko nufinka yara ka mayar da mu da za ka ce masu ƙwacen waya sun tare ka mu ƙu yin bincike? Yanzu dama Saddam da 'yar daba kake zaune? A ce yarinya ƙarama kuma mace har ta san ta cakawa mutum wuƙa? Wallahi kashe ka ma ta so yi, don haka dole sai an hukunta su, ba don Babanku ya hana ni zuwa ba ma da da ni za a tafi gidan nasu". Sadam hankalinsa ya tashi, ya ji sam ba ya so a taɓa Sayyada, ya ce"Momy don Allah kar ku yi wani yunƙuri, wallahi laifina ne, sai da ta ce na sake ta na ƙi, kuma dama tana da matsalar aljanu, na tabbata su ne suka tashi". Ta ce"Au! Lallai ka yi nisa, anya wannan yarinyar da iyayenta ba su asirceka ba kuwa? Anya kana cikin hayyacinka Saddam? Mace ta yi yunƙurin kashe ka ka dinga kare ta? Ai kuwa idan wannan so ne, Allah wadaran soyayya wallahi". Tana haki ta ce"Yanzu an tafi gidansu da hukuma, sai ka tashi ka je ka dakatar da su tun da rayuwarka ce idan an taɓa ka za ta mutu". Ta fita ta bar shi a ɗakin, ya ji sam zuciyarsa babu daɗi, tun da ya sake ta a ganinsa ya kamata ko ma me ta yi masa su rabu da ita kawai. Ya ɗauki wayarsa ya kira layin babansa, a raunane ya ce"Abba, da gaske an tafi za a kama Sayyada" Abba ya ce"E hakane". Sadam ya ce"Don Allah Abba kar a kama ta, ai ni ta yi wa, kuma na yafe mata, ku bar ta ta ji da sabuwar rayuwar da za ta faɗa". Abba ya ce"Ba zai yiwu ba, wannan yunƙurin kisan kai ne ta yi, kuma hukuma ta riga ta shiga maganar don haka yanzu komai yana hannunsu, sannan ina ba ka umarnin ka saki yarinyar nan, domin idan ba ka san ciwon kanka ba ni na san ciwonka, ba zai yiwu ka zauna da wacce take farautar rayuwarka ba". A sanyaye ya ce"Ai na sake ta tun a jiyan, amma don Allah Abba a kashe case ɗin, wallahi ba ta da me tsaya mata, ni na yafe mata". Abba ya ce"Sadam kenan, wannan ya nuna har yanzu kana sonta, ƙila ma ba a son ranka ka sake ta ba, to shikenan ta je dan kanta, amma kamar yadda na faɗa maka case ɗin yanzu yana hannun hukuma, idan ka samu lafiya sai ka faɗa musu ka yafe". Ya ce"To na gode Abba, ko zan samu lambar wanda case ɗin ke hannunsa?" Ya ce"A'a ba za ka samu ba, tana can a kulle, kuma ban amince maka ka sa a yi belinta ba, ko ka yi magana da wani ɗan sanda, har sai ka samu lafiya an sallame ka daga asibiti". A sanyaye ya ce"To". Jikinsa ya yi sanyi sosai, jin wai Sayyada tana kulle, ya lumshe ido yana godewa da Allah da ba ta kashe shi ba, yana jin shigowar Safna, amma ya yi kamar mai bacci, tun ɗazu take ta zagin Sayyada da tsine mata, ya rasa yadda zai yi ta fahimci ba ya so, ya san inda a da ne da cewa za ta yi tsautsayi ne, don a baya kafin aurensu ba ta ganin laifin Sayyada, amma tun da aka yi auren ta canza wasu halayen nata. SAYYADA Na ci kuka sosai a wannan daren, na zubewar cikina, da safe aka sallame mu muka koma gida, aka ce a je gidana a kwaso min kayan sakawata, amma fir na ƙi, tun da na san abin da na aikata, sai kayan ƙanwar Anisa na saka da na yi wanka, na kwanta lamo kamar mara gata, wajen goma na safe sai ga shi Baba ya kira baban su Anisa, ya ɗauka ya tambaye shi ina gidansa? Ya ce ina nan, bai ce komai ba ya katse kiran, babu jimawa kuma aka fara sallama daga waje, shi ya fita ya duba, ganin 'yan sanda gabansa ya faɗi, suka ce sun zo tafiya da ni, ya tambaye su me na yi? Suka ce idan an je office ma ji, yana shigowa ya faɗa na fashe da kuka ina roƙon don Allah kar su bari a tafi da ni, Baba ya ce"Kin yi laifi ne?" Na ce"E, na sokawa Sadam wuƙa a cinya, amma wallahi tsautsayi ne". Duka gidan aka ɗauki salati ana sallalami, haka aka ja ni aka tafi da ni, ina ta gursheƙen kukan nadama. Ina ji ina ga i aka tura ni cikin sell, tsorona ma kar Baba ya ji ya ƙara linka fushinsa a kaina, wallahi da gaske na yi nadama, don ma dai ana ba ni abinci mai kyau, kuma ba a dake ni ba sai tsangwama da hantara, ga sauro a wajen ba na iya bacci mai daɗi, komai dai ba ya yi min daɗi, sai da na yi sati biyu a wannan halin sannan watarana aka fito da ni, aka faɗa min Sadam ya ce ya yafe min, tun da shi aka cuta kuma Iyayensa da suka kawo ƙarar sun ce ya yi yadda ya tsara shikenan za a sake ni, amma sai na je na ba shi haƙuri, yana gida yau an sallame shi, na ce to, jikina duk a mace. Haka suka tisa ni a gaba har gidan Sadam, inda yake zaune da Safna, ban ma san inda gidan yake ba sai yanzu, a tare da ni akwai Baban Anisa, ko na ce babana a yanzu, shi ma jikinsa duk ya yi sanyi, kuma da alama ya a fushi da ni, domin ban gan shi ba sai yau, tun da aka rufe ni ba a bar kowa ya gan ni ba. Ni ce ta farkon shiga falon, tun da tusa ni a gaba suka yi, ina shiga idona ya sauka a kan Sadam, dake zaune a falon yana waya, yana sanye da jallabiya, zuciyata ta buga, na shiga tunano irin cutar da ya yi min ba alkhairinsa ba, ɗaya daga cikin 'yan sandan ya daka min tsawa da faɗin"Ki durƙusa ki yi abin da ya kawo ki!". Na lumshe ido hawaye ya sakko min, sannan na durƙusa ɗin kamar ɗalibi a gaban malami, tun da nake ban taɓa durƙusawa Saddam ba sai yau, suka shiga gaisawa da mutanen, ni kuma kaina a ƙasa, suka gama Baba ma ya ba shi haƙuri sosai, kafin falon ya yi shiru, wannan ɗan sandan me rawar kai da fala-falan kunne ya sake yi min tsawa kamar zai hau kaina ya ce"Ba za ki yi abin da ya kawo ki ba? Stupid!". Sadam ya ɗaga masa hannu alamar ya rabu da ni. Jikina ya hau rawa, da muryar kuka na ce"Na yi kuskure, don Allah ka yi haƙuri ka yafe min". Ya kalli mutanen falon ya ce"Ku ɗan ba mu waje". Duk suka fita, ya rage daga ni sai shi, ya zuba min ido yana kallona, kafin ya ce"Sayyada, da gaske za ki iya kashe ni inda ban sake ki ba?" Na girgiza kai alamar a'a, na ce"Ka yi haƙuri don Allah, barazana ce, da kuma zugar zuciya". Bai ce komai ba, kallona kawai yake yi, duk na tsargu kunya ta kama ni, ya sauke ajiyar zuciya ya ce"Allah ne shaidata, na yafe miki ko da ba ki nemi yafiyata ba, amma kina da zuciya mai duhu Sayyada, ki yawaita addu'a Allah Ya raba ki da sharrin zuciyarki, Allah Ya sa ki fi ƙarfinta, domin da alama zuciyarki ta fi ƙarfinki". Sai na rushe da kuka sosai, ya ce"Shikenan za ki iya tafiya, Allah Ya kyauta". Na ci gaba da kukan ban ko motsa ba. Ya ce"Sayyada akwai wata matsalar ne? Ko Baba bai karɓe ki ba?" Na ce"Ai ni da kai mun san ba zai karɓe ni ba, amma ba wannan nake yi wa kuka ba, a ranar da abun ya faru na yi ɓari, ashe ina da ciki ban sani ba". Shi ma ya ji zuciyarsa ta doka, ya ce"Ciki? Da gaske kin samu ciki kuma ya zube?" Na jinjina kai ina cigaba da kukan na ce"Wallahi da na san ina da shi da na haƙura, da ban aikata komai ba, don Allah ka yafe min, mun rasa jininmu ta sanadina". Ya sauke numfashi ya ce"Babu komai, haka Allah Ya tsara, kenan hakan yana nufin kin gama idda ko?" Ban ba shi amsa ba. Ya ce"Kin gama idda Sayyada, shikenan mun yi rabuwa ta gaske, Allah Ya ba ki kalar mijin da kike so, na yafe miki, ban sani ba ko za ki iya yafe min tarin cutarwar da na yi kiki?" Na ce"Na yafe maka, ni dama fatana na yi nesa da kai, hakan ne kawai zai saka na manta". Ya yi guntun murmushi ya ce"Shikenan, Allah Ya yafe mana bakiɗaya, za ki iya tafiya". Na tashi na fara tafiya ina share hawayen rashin dalili, har na je ƙofa ya ce"Sayyada". Na tsaya ban amsa ba, ban juyo ba, ya ce"Idan kina neman taimako ko na kuɗi ko wani abun za ki iya tuntuɓata kin ji?" Na gyaɗa masa kai alamar na ji, na fita daga ɗakin. Su 'yan sandan shiga suka yi wajensa, ni kuma muka fice daga gidan ni da Baba, a adaidaitasahun ma yana ta yi min faɗa da nasiha, ina ta kuka da ba shi haƙuri, tun da yanzu shi ne gatana, idan ya yi fushi da ni ina zan kama? Littafin nan na kuɗi ne a Kan Naira 700 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 [05/10, 7:51 pm] Sadiya Abdulrazak: 13 Haka muka koma gida jikina a mace, nan na shiga roƙon Baba ina cewa"Don Allah Baba wannan abun da na yi wa Saddam ya zama sirrinmu, don Allah kar a bari Babana ya ji". Baba ya ce"Ai ya ma riga ni ji, kuma wannan ya sake fusata shi sosai a kan lamarin, amma ni a shawarata duk da ya ce kar ki sake taka gidansa, to kar ki biye masa, duk ranar Juma'a za ki dinga zuwa ki gaishe shi ko ba zai amsa ba, zancen kayanki na gidan mijinki kuma za mu yi magana da mijin naki idan ya sake warwarewa sai a kwaso miki idan ajiyewa za a yi ga ɗaki nan, idan siyarwa za a yi sai a siyar, tun da kin gama iddarki". Na share hawaye na ce"To Baba, na gode". A ranar da yamma sai ga Mama ta zo gidan, ita ma sosai ta nuna ɓacin ranta kan abin da na aikata, har ta zubar da hawaye, wanda ya sake sawa na ga tabbas na aikata laifi mai girma, ina kuka na ce"Mama ki yi haƙuri, don ki daina yi mini kuka, na yi kuskure, ku yafe min". Ta ce"Sayyada kar ki saka na fara nadamar haihuwarki fa, wallahi ban taɓa tunanin ko ɓera za ki iya rutsawa ki cakawa wuƙa ba, sai ga shi kin aikata haka ga mijinki, Sadam yana sonki na sani, kawai na tsane shi ne saboda ina ganinki a cikin ƙunci, an yi ya fi dubu namiji ya lalata mace, idan aka tilasta ya aure t sai wulaƙanci da muzgunawa su biyo baya, shi yasa na yi zaton ke ma haka ne ya faru da ke, amma ba haka ba ne ke ce kika riƙe shi, yanzu ƙiyayyar har ta kai ki ɗauki wuƙa ko caka masa? Hmm shikenan tun da auren ya mutu, Allah Ya ba ki wani na gari". Na girgiza kai na ce"Mama ni fa ba zan yi aure ba, na haƙura kawai". Ta ce"Ai kuwa aure ya zama dole, sai dai idan ba ki samu wanda zai aure ki ba". Ta shiga yi min nasiha, ta daɗe a gidan, sai bayan magriba ta tafi, ta bar ni da kewarta, da kewar gidanmu, da ɗakinmu, yau ba ni da damar zuwa gidan da aka haife ni na kwana duk silar Saddam, nan take na sake jin tsanarsa a zuciyata, da gaske na yi nadamar aikata masa wannan abun, amma har yanzu na tsane shi, kuma gani nake laifinsa ne, tun da shi ya ƙi sakina ai. Haka na gyara zaman gidan Baba, Wanda nake jin a yanzu ya fi Babana sona, tun da shi ya yi min uzuri, nasiha ce kullum tsakanina da shi da shawarwari na ƙwarai, duk ranar Juma'a ina zuwa gidanmu na gaida su, kuma Baba yana amsawa, amma daga nan bai taɓa ce mini komai ba, na gode Allah ma da bai hana ni shiga gidan ba. Wallahi duk a zatona Sadam ba zai iya haƙura da ni tafarat ɗaya ba, na zata zai ta bina ne yana damuna da waya a kan na yarda a mayar da aurenmu, sai kuma wannan halin ko'inkula ɗin da ya nuna ya dame ni, sautari idan ina zaune sai na dinga tunanin shi, na dinga tuna ko ke yake yi yanzu? Ko yana zuwana gidana ya kwana ko kuwa shikenan ya zama na amaryar gabaɗaya, ƙila ma har ta samu ciki yana can yana zumuɗi, sai na ji haushi ya kama ni, tsakani da Allah na tsani matar Sadam, ina matuƙar jin kishinta har yanzu, gani nake ta cuce ni, domin da bai ɗakko zancen ƙara auren ba da tuni yanzu muna ta rayuwarmu cikin farincin kamar yadda muka saba, ina nan da implant ɗina a jikina, Safna ta tarwatsa komai. Wataran kuma sai na yi tunanin ko ita ma idan ya neme ta ba ta ba shi haɗin kai ba yana yi mata fyaɗe? Sai wata zuciyar ta ce ai ita ba za ta ƙi ba ma, na san ma jarababbiya ce irinsa, haka dai kullum ba ni da tunani sai na shi, na saƙa wannan na kunce wancen, har na zo ma ina jin haushin kaina, tun da ina ruwana da shi? Yanzu ai ba mu da wata alaƙa kuma. Gani nake ko cewa da ya yi idan ina buƙatar taimako na tuntuɓe shi ya faɗa ne kawai, ba don da gaske zai taimaka min ɗin ba, musamman idan na tuna lokutan baƙinciki da suka wanzu a zamanmu, wanda suka shafe na farincikin. Watarana kamar a mafarki sai ga kiran Sadam a wayata, gabana ya faɗi rass, na shiga tunanin abin da zai faɗa min, na dai yi shahada na ɗauka da sallama, a raina ina tunanin ko dai yana can yana kewata ne, ƙila ya kasa jurewa shi yasa ya kira ni zai roƙe ni, ya amsa sallamar, muka yi shiru na ɗan lokaci, ban gaishe shi ba ma, sai shi ya ce"Sayyada mun tashi lafiya?" A takaice na ce"Ƙalau". Ya ce"Ma sha Allah, ya zawarci da zawarawa? Da fatan dai kasuwar tana kyau". Raina ya ɓaci nan take, sam ban tsammaci maganar nan daga bakinsa ba, ni zai rainawa hankali? Sai kace wacce ta kasa haja zai tambayi ya kasuwar zawarawa? Wannan ai wulaƙanci ne, ban gama mamakin zancen ba ya ce"Uhm Sayyada? Akwai kasuwar kuwa?" A fusace na ce"Ka kira ni ne saboda ka wulaƙanta ni? To kasuwa Alhamdulillah! Ai rayuwar zawarci ta fiye min rayuwar gidanka sau dubu, don haka zawarawa da zawarci Alhamdulillah!". Ya yi yar dariya ya ce"Mai da wuƙar, ni dama tambaya ce, na kira ne na tambaye ki yaushe za a kwashe kayanki daga gidan nan? Ina so zan saka 'yan haya ne". Na tuna kamar akwai lokacin da ya ce ya bar min gidan nan da muke ciki, sai kuma na kasa tuna yadda maganar take, amma na ji babu daɗi da na ji wai ya kira ne don ya faɗa min na kwashe kayana, ta tabbata dai aure ni da Sadam ya kare, Kodayake ai hakan nake so dama. Na ce"Zan faɗa musu za a zo a kwashe". Ya ce"To a hanzarta don Allah". Na kashe kiran ban ba shi amsa ba, takaici na ji ya kama ni, haka dai na faɗawa Umma saƙon shi, sosai na ji Baba ya burge ni da aka kwashe kayan a ranar, aka zo aka jibge su a gida, Baba ne ya ba da shawarar kar a siyar, idan na samu wani mijin kawai sai a yi auren cikin sauƙi. A kwana a tashi na ɗauki watanni biyar a gida, a hankali kuma sai hankalin mazan unguwarmu da kewaye ya fara yo wa kaina, sai ka ji ana sallama da sayyada, sai na fita na ga wani gajarabul ɗin, ya cika ni da zantukan banza, to wallahi a zancen banza nake jinsu, saboda ni cikin wanda suka taɓa zuwa wajena babu wanda ya yi min, duk ba su kai Sadam class da gayu ba, duk da akwai wanda suka fi shi kyau, amma ni ba kyau nake dubawa ba, don da shi ne da ban zaɓi Sadam ba, a ya yi wuta mutum ya yi zuwa uku, zan saita masa hanya da kora da hali, idan ma bai ji ba ko an yi sallama da ni sai na ƙi fita, kafin Baba ya fara matsa min, a dole nake fita ko ba na son mutum, kullum nasihar Baba ita ce na tsayar da wani cikin manemana na yi aure, shi ne mutuncina kuma gatana, yana saka ran idan na yi auren na auri miji na gari Baba zai iya yafe min, don har da ganina tare da Sadam a ƙara hasala shi, a hankalin ni ma na fara son na yi auren, amma na rasa wanda zan zaɓa, wallahi duk ba su yi min ba. Akwai wani Sulaiman ɗan layinmu, ya fi kowa naci, adaidaitasahu yake ja, kuma ko fili ba shi da shi, lissafinsa a gidan haya za mu zauna, yana da nutsuwa sosai, ga shi ya iya magana, to shi dai talaucinsa ne ya yi min yawa, har ga Allah zan ji takaicin a ce na fito daga danƙareren gidan Sadam har da mai gadi, na ƙare a gidan haya, ban da haka da zan iya daurewa na aure shiga shi. Sai kuma wani Abubakar, shi kuma yana da rufin asiri ba laifi, duk da bai kai Sadam ba, yana da gidansa ɗan madaidaici, matsalarsa ɗaya ya taɓa yin aure yaransa biyu matar ce ta rasu, kuma shi a tsarinsa idan an yi auren ni ce zan riƙe masa yaran, sai nake ganin kawai zai aure ni ne saboda na zama mai raino, don haka shi ma nake ganin ba mijin aure ba ne. Aliyyu shi kuma saurayi ne, yana da gidansa mai ɗaki biyu da kitchen da banɗaki, yana sona sosai, sai dai yana zuciya da saurin fushi, da fari na so na yarda da shi, amma tun da na ga fara yi min faɗa idan ya kira ni ya ji ba na gida sai na samawa kaina lafiya, sai ya ce wai me yasa ban faɗa masa zan je wajen kaza ba? Nan dai na gane irin Sadam ne, kuma idan ya samu damata tsaf zai mayar da ni ruwa, shi yasa duk nake ta juyi don cikinsu babu na zaɓa. Ana haka ne Anisa ta haɗa ni da yayan mijinta, ya rabu da matarsa yaransu uku, ina jin haka na ce a'a, bai yarda ba sai da ya fara zuwa, Baba ya ce shi dai ya yaba da shi, na dai fara kula shi ba don ina jin zan iya aurensa ba, amma da yake Alhaji Shamsi ya isa soyayya da tsara zance sai ya fara jan ra'ayina cikin hikima, ya fi Saddam kyau, sai dai ya fi shi shekaru ma, amma ba girma ta yi can-can ba, sannan gidansa babba ne, kuma yana da kuɗi sosai, har ya fi Sadam, sannan yana da kyauta, ya iya tsara ni, tun ina jin wasu halayensa ne kawai suka fara birge ni har na zo na yarda ƙaunarsa nake yi, kuma har zuciyata na yarda da aurensa, har na ji zan iya riƙe masa yaransa, kuma ma yana ta ƙarfafata ya ce akwai mai kula da su, idan an yi auren ma ita za ta cigaba da kula da su. Da kullum idan na zauna na yi ta tunanin rayuwata ta baya da Sadam, amma yanzu rayuwata ta gaba da Alhaji Shamsi kawai nake hasashowa, wanda na yi wa lakabi da Alhajina, kowa ya san ni bayan mutuwar aurena ya gan ni a yanzu zai gane na samu kwanciyar hankali, Mama ta san da ina son Alhaji kuma ita ma ta yi na'am da shi, Baba ne dai ban sani ba ko ta faɗa masa. Wata ranar Juma'a Alhaji yake ce min na faɗawa Bana ranar Lahadi za a zo neman aure, idan an ba shi sai a saka rana tun a wajen, ba ya fatan abun ya wuce watanni biyu, shi ma don yana son ya yi gyaran gidan ne, murmushi na yi, wani daɗi ta lulluɓe ni na ce"Alhaji yanzu mene ne abun gyara s gidan nan namu?" Kasancewar ya tura min vedion gidan, kullum sai na kalla, na dinga tsara ga falona ga inda za mu dinga hutawa ni fa shi. Ya ce"Za a canza fenti, ƙofofin ma za a canza wasu, ai ke ta musamman ce Sayyadata don haka dole na yi miki gyaran da zai dace da ke". Na yi murmushi na ce"Na gode sosai". Ya ce"Wai lefe zan yi miki ma ko gara kuɗin?" Na rufe fuska ina juya masa baya alamar kunya, ya yi dariya ya ce"Sayyada kenan, wai kina nufin kunya kike ji kamar wata buduruwa? Kodayake a wajena ke sabuwa ce dall". Na ce"Ba wani nan, kawai dai kana koɗa ni ne". Ya ce"Wallahi har zuciyata gani nake kamar buduruwa xan aura, ke ma ki manta da wanann ƙaton cikin nawa ki bar shi a saurayi za ki aura, da sai mun fi more rayuwar auren". Na ce"Ai dama kai saurayi ne a wajena, shi yasa ma idan muka yi aure..." Sai kuma na kasa ƙarasawa na rufe fuska. Ya ce"Ƙarasa mana". Na ce"A'a mu bar zancen". Ya ce"To ina bin ki bashi, za ki faɗa min ta chatting ko da a rubuce ne". Na ce"Na yarda". Ya ce"Lefen zan yi ko kuɗi?" Na ce"Duk abin da su Baba suka ce". Ya ce"To ma sha Allah, sai ki sanar musu kar ki manta, Jibi in sha Allah za a zo, na gaji da gwaurancin nan". Muka sha firarmu cikin nishaɗi ya tafi, ina shiga kuwa na faɗawa Umma saƙonsa, na yi murna sosai, don ana so a ga na yi aure ina ɗakina, a ranar na yi ta jiransa ya zo online mu yi fira kamar yadda muka saba kafin mu yi bacci sai na ji shiru bai yi min magana ba, na duba na gan shi online, na yi masa sallama amma har bacci ya fara kama ni bai duba ba, raina ya ɓaci, jira nake gobe ya kira ni na ji dalili, sai na yi masa daru sosai kafin ya shawo kaina. Abun mamaki washe gari tun safe nake jiran wayarsa shiru bai kira ni ba, na wuni suƙuƙu ina tunanin dalilinsa, ga shi ina ganinsa online har yana status ballantana na ce ba lafiya ba, haushi na ji sosai, shi yasa ni ma na ƙi kiransa, haka muka sake kwana bai neme ni ba, sai ranar Lahadi da asuba na gaida Baba yake ce min na tambaye shi ƙarfe nawa masu tambayar za su zo, kuma wace amsa za a ba su ina son shi? Kaina a ƙasa na ce"To ban dai sani amma zan tambaye shi ɗin". Ya sake cewa"Kina son shi?" Na ce"E Baba". Ya ce"To ma sha Allah, Allah Ya tabbatar mana da alkhairi". Na tashi na koma ɗaki, sai na yi masa text massage na ce"Assalamu alaikum, Barka da safiya, Baba ya ce na tambaye ka ƙarfe nawa za su zo?" Babu jimawa ya dawo min da amsa ya ce"Ki yi haƙuri Sayyada, sun fasa zuwa". Gabana ya faɗi, na rubuta masa,"Me yasa?" Ya dawo min da amsa"Saboda na fasa aurenki". Hannuna ya ɗauki rawa, na saki wayar zuciyata tana bugu, nan take na shiga firgici, sai ga kiransa, na ɗauka da sauri da rawar murya na ce"Alhaji ba na son irin wannan wasan". Ya ce"Sayyada kina tunanin son da kike yi mini ya fi wanda nake yi miki ne? Ina son ki sosai, idan haka ne me yasa zan yi wasa da wannan maganar mara daɗi? Da gaske na fasa aurenki". Kamar zan yi kuka na ce"Me yasa? Me na yi maka don Allah?" Ya ce"Shawara mahaifiyata ce, kin san kuma ba za ta ba ni gurguwar shawara ba, shi yasa ko tambayarta dalili ba na yi, amma wannan karon na san dalilin ma". Na ce"Me na yi mata?" Ya ce"Ba ita kika yi wa ba, kanki kika yiwa". Na yi tsam ina tunanin manufarsa, ya ce"Na so ki ba tare da sanin ainahin wace ce ke ba, sai yanzu kawai na samu labarin wace ce ke, ban san kin yi rayuwar zina da tsohon mijinki kafin aurenku ba, da ke da Anisa ce min kuka yi zumunci ne kawai ya sa kike zaune a gidan yayan babanki, ashe Babanki sallama ki ya yi ya ma kore ki daga gidansa, sannan kuma duk macen da za ta iya cakawa mijinta wuƙa ba matar aure ba ce, inda na san duka wannan da ba zan saka ki ko a ƙofar zuciyata ba ne, ina sonki Sayyada amma za mu rabu dole, ko Mama ba ta ba ni shawara ba ni ma ba zan iya auren irinki ba, tsira da rai ya fi tsira da dukiya, bis salam". Ya kashe wayar, haka na daskare da wayar liƙe a kunnena, bugun numfashina sai hawa da sauka yake, abubuwa suka shiga dawowa kwanyata, na saka kaina a cinya na fashe da kuka mai ƙarfi, kukan da har Umma da Baba sai da suka jiyo, Umma ta taho da sauri tana tambayata dalili, na ce"Wai ya fasa, Umma ya ce ya fasa aurena, wai ya ji labarin mahaifina yana fushi da ni ya sallama ni na shiga uku!". Na sake rushewa da kuka, Suna rarrashina kamar suna lakaɗa min duka na ƙi dakatawa da kukan, sai da na yi mai isata, sannan Baba ya zauna ya dinga yi mini nasiha da son nuna min hakan shi ya fi alkhairi, na dage da neman zaɓin Allah kawai, zai kawo wanda zai aure ni ko da ya ji labarin abin da na aikata. 08028966015 [06/10, 6:18 pm] Sadiya Abdulrazak: LITTAFIN KU YI MANA ADALCI NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, IDAN KINA JIN DAƊIN KARANTA SHI NI MA KI YI MIN ADALCI KI BIYA NI KUƊIN KARATUNA. 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 14 A ranar dai na shiga tashin hankali sosai, sai na ji kamar ma sai yanzu ne na fara son Alhaji Shamsi, na rasa yadda zan yi, na dinga kiran shi ba ya ɗauka, ƙarshe ma na daina samunsa, da alama ya yi blocking ɗina har ta whatsApp, ranar Juma'a da na je gida Mama ta dinga ba ni haƙuri, da nuna min wannan shi ne illar abin da na aikata, zina tana da rabo mai girma, sannan ga illar biyewa sharrin zuciya, yanzu zai yi wuya wani ya ji na cakawa mijina wuƙa ya yarda ya aure ni, na riga na yi wa kaina baƙin fenti, ranar na ci kuka na gode Allah, Baba ba ya nan, ban tafi ba har dare ina jiransa, da ya dawo na gaishe shi ya amsa babu walwala, na fara roƙonsa ya yafe min, ya ɗaga min hannu kafin ya nuna min hanyar fita a fusace ya ce"Sayyada tashi ki bar gidan nan, kar ki sake neman yafiyata, na faɗa miki ba zan yafe miki ba sai ranar da na ga gawarki, kuma idan kina da wani wanda kike so bayan wanda ya fasa ɗin, ki tsayar da shi ki yi aure, wannan umarni ne na ba ki, wanda idan kika cika zan iya duba yiwuwar yafe miki ko kuma na tsaya a kan bakana". Komai nawa ya tsaya cak, da gaske idan na yi aure Baba zai iya yafe min? Idan kuwa hakane ya zama dole na yi aure, domin yanzu ba ni da babban buri sai ganin Baba ya yafe min mun dawo rayuwa kamar baya, a raunane na ce"In sha Allah zan samu wani, Baba ku taya ni addu'a Allah ya ba ni na gari". Bai amsa ba, na fice daga gidan ina waiwayensa. Tun daga ranar na sakawa raina son aure, na fara soyayya da Sulaiman wannan saurayin mai adaidaitasahun, wanda na ce zai ajiye ni a gidan haya, yanzu na sauke farashi ji nake ko a kango zai ajiye ni zan aure shi indai Baba zai yafe min, mun kai wata biyar muna soyayya, yana ta tara tara kuɗin auren, ya ce kullum dubu ɗaya yake ajiyewa, sannan ya samu ya haɗa dubu ɗari da hamsin, zai kawo kuɗin aurena, wannan ɗari da hamsin ɗin a ciki akwai sadaki da kuma dukiyar aure, zuwa lokacin na koyawa kaina son Sulaiman, burina a yi auren kawai, duk da ina tunanin fuskantar ƙalubale ko daga wajen mahaifiyarsa ne, nahaifinsu ya rasu, kuma shi Sulaiman ɗin ne mai riƙe da gidan nasu, mahaifiyarsa da ƙannensa uku mata ɗaya namiji, yanzu zai yi aure, shi ma hidimar gidansa ta hau kansa, ko yaya ne idan ya aure ni dole zai iya ragewa gidansu wata hidimar, tun da samun nasa ba ƙaruwa zai yi ba, da yawa haka tana faruwa, kuma laifin matar da ta aura ake gani, ba a duba nauyi ne ya ƙaru damu bai ƙaru ba, dole za a ga hakan, sai a ce mace ce ta mallake shi, ta hana shi hidimtawa iyayensa, sai ƙiyayya ta shigo ciki a takurawa yarinya a hana ta zama lafiya a gidan mijinta, ina jiyewa kaina wannan abun. Wani lokacin sai na dinga tunanin shin shi Sulaiman ba shi da masaniyar wannan abubuwa da na aikata? Saboda ban ga alamar hakan ba ko da wasa, haka aka kawo kuɗin aurena, aka saka rana sati huɗu masu zuwa, ya ce min zai fara fafutukar neman haya tun yanzu, tun da aka saka ranar na ji shiru babu alamar Sulaiman ya ji labarin nan nawa mara kyau, sai zuciyata mara adalci ta ɗarsa min zargin Anisa, kawai na fara tunanin baƙinciki take yi min shi yasa ta faɗawa Alhaji Shamsi wannan tabon nawa, wata zuciyar ta ce min idan ba ta sona da shi tun farko me yasa za ta haɗa ni da shi? Muguwar zuciyar ta bawa kyakkyawar amsa da faɗin so take ta tozarta ki, so take a hankali kowa ya sani, ko kuma ta ga ya fi mijinta kuɗi shi ne take yi miki hassada, wallahi kawai sai na yarda da zuciyata, ba sai na ɗauki fushi da Anisa ba, dama ita ce abokiyar shawarata ko chatting, na yi mugun jan baya da ita, ko gidan ta zo na yi ta haɗe rai kenan, tun tana ja na a jiki har ta gane akwai wata a ƙasa, takanas ta zaunar da ni ta tambaye ni me ta yi min, ba ce babu komai kawai yanayi ne, da Umma ma ta fuskanci akwai wani abu ita ma ta zaunar da ni ta tambaye ni ko akwai laifin da Anisa ta yi min? Na ce babu, haka suka rabu da ni ina ta fushi da ita, shi yasa nake ƙara son Sulaiman, har alla-alla nake a yi auren ta mutu da baƙinciki tun da dai hassada take yi min, da baƙinciki, ƙila zamana a gidansu ne ma yake ƙona mata rai, oh mutum sai a bar shi. Aurenmu ya rage sati ɗaya, Sulaiman ya zo zance, ya kira ni ya ce yana ƙofar gida, na fita, sai na gan shi a birkice ba kamar yadda na saba ganinsa ba, na ce"Yaya Sulaiman lafiya?" Ya haɗe gira ya ce"Sayyada da gaske kin yi wata rayuwa kafin aurenki da wanda kika aura? Da gaske kin caka masa wuƙa?" Na ji kalamansa kamar saukar guduna, gabana ya ba da rass, na kasa cewa komai, ya ce"Shirunki yana nufin tabbatar min?" Na gyɗa masa kai alamar e, sannan na ce"Amma wallahi ƙaddara ce, komai ya faru ba da son raina ba ne, don Allah ka yi mini uzuri Yaya Sulaiman, ni mutum ce kamar kowa, zan iya yin kuskure". Ya ce"Hmm, Sayyada kenan amma dai na yi mamaki sosai wallahi, ban taɓa zaton za ki aikata ba, ashe ke sumumu kasau ce? Micijin sari ka noƙe ce ke?" Na ce"Ƙaddara ce wallahi, kuma na yi nadama, ko da wasa ba zan sake gwada aikatawa ba". Ya ce"Ki yi haƙuri Sayyada, mahaifiyata ce ta yi mini umarnin na fasa aurenki, kuma ba na jayayya da maganarta, ta ce har gida aka je aka faɗa mata, don haka ko da zarginki ake yi ba ki aikata ba sai na fasa auren, ballantana ma ga shi kin tabbatar min ba zargi ba ne". Na fara kuka mara sauti, na ce"Don Allah ka yi mini adalci, wallahi tsautsayi ne, mu je na roƙi Umman, don Allah kar ka fasa aurena ka tona min asiri, yanzu ido da hankali zai dawo kaina a fara tunanin mene ne dalilin da yasa ake fasa aurena". Ya ce"To a shawarce kawai duk wanda ya zo miki da batun aure ki dinga faɗa masa tun kafin tafiya ta yi nisa, idan ya ji zai iya shikenan, idan ba zai iya ba kin ga sai ya tafi tun ba a gane ki da shi ba". Na ce"Kenan ni da kaina zan dinga yamaɗiɗi da labarina? Ba zan iya haka ba". Ya ce"To Allah Ya kyauta, sai ki sanarwa da iyayenki zuwa wani satin su dawo min da kuɗin aurena tun da ban sani ba ko an taɓa shi, na bar ki lafiya". Ya wuce ya bar ni tsaye da ƙunar rai, sai na ji kamar na ɗora hannu a ka na rushe da kuka, ya ce har gida aka je aka faɗawa babarsa, hakan yana nufin mace ce ta je ta kai zancen kenan? Idan har haka ne to kuwa tabbas Anisa ce, nan take na ƙara jin tsanarta ta linku a zuciyata. A ranar birkicewa na yi, na dinga kuka mai sauti kamar mai aljanu, don Baba tofa min addu'a ya dinga yi, yadda na ga rana haka na ga dare, sassafe ko karyawa ban yi ba na tafi gidanmu, durƙusawa na yi a ƙofar ɗakin Baba ina ta kuka sosai, duk yadda Mama ta yi da ni na tashi ƙi na yi, har dai kukan ya ishi Baba, ya fito fuskarsa a haɗe ya ce"Ke uban wa kika zo kika saka a gaba da kuka haka?" Cikin kuka na ce"Baba shi ma ya fasa". Ya ce"Idan ya fasa sai me? Laifin wa? Dama duk me hankali ai dole ya ji shakkun aurenki". Na ce"Don Allah Baba ka yafe min, ƙila hakan zai saka na samu sassaucin wannan abu da yake bibiyata". Ya yi tsaki ya koma ɗaki, na ƙi tashi daga wajen, sai da ya na kusa awa ɗaya a wajen, sannan da ƙyar Mama ta zo ta ja ni zuwa ɗaki, duk yadda ta so na ci abinci na kasa ci. Baba sammakon zuwa kasuwa ya yi niyya yau ɗin, amma sai ya kasa, yau dai ya ji tausayin Sayyada, ya gane da gaske ta yi nadama, amma ba zai nuna mata ya yafe mata ba har sai wani lokaci, a fili ya furta"Astagfirullah, Allah na tuba Ka yafe ni, idan saboda fushina dake kan Sayyada ne ta kasa auruwa Allah ka shaida na yafewa ɗiyata Sayyada, Allah ka shiga lamarinta ka ba ta miji na gari". Tun daga wannan ranar na sake zama silent, na daina kula samarin da a kullum dai wani ya doko na sallama, na yi alƙawarin ba zan sake saka wani a raina ba, ya zo ya azabtar da ni ya ce ya fasa daga ƙarshe, sai na kama sallaya, Qur'ani da kuma carbi suka zama abokan rayuwata, da dare na yi sallah, da rana na yi karatun Qur'ani da istigfari, cikin lokaci ƙanƙani na fara jin sanyi a zuciyata, ga kuma nutsuwar gangan jiki. Wata ɗaya da faruwar haka, wataranar Juma'a ina gidanmu a kwance ina istigfari sai ga Baba ya dawo daga masallaci, na yi mamakin jin yana tambayar Mama dake tsakar gida ni, ya ce"Ina Sayyada, ta zo?" Mama ta ce"Ta zo, tana ciki ina ga bacci take". Na taso da sauri na fito ina cewa"Mama idona biyu". Baba ya ce"To ma sha Allah!" Ya zauna a tabarmar da Mama ke zaune ni kuma na tsugunna daga gefe, ya ce"Sayyada a yau na yanke wani hukunci a kanki ba tare da saninki ba, sai dai ban sani ba ko za ki amince da hukuncina?" Gabana ya faɗi rass, na ce"Baba kana da cikakken iko da ni, na amince ko ma mene ne". Ya fito da kuɗi daga aljihunsa, sannan ya ciro wata leda, ya miƙo min kuɗin ya ce"Ƙirga su, dubu ɗari ne". Na karɓa hannuna sai rawa yake na fara kirgawa, ban yi nisa ba na ce"Baba ba sai na ƙirga ba, tun da ka ce ɗari ne haka ɗin ne". Ya turawa Mama ledar ya ce"Wannan goro ne da alawa a ciki, a yau na aurawa wani bayan Allah Sayyada, wanda na yaba da halinsa, kuma na faɗa masa tabon da yake bibiyarta, amma ya ce ya ji ya gani, sai ku yi haƙuri idan na yi muku laifi ke da ita bakiɗaya". Tun da ya ce ya aura min wani na ji kamar zuciyata ta tsinke, fargaba ta shige ni, na fara tunanin shin wane ne wannan da ya ce ya ji ya gani tun bai gan ni ba? Wane ne wannan da Baba ya yaba da shi ya ga dacewar aura mini shi ba tare da amincewata ba?" Mama ta ce"Ikon Allah, amma wane ne shi?" Baba ya ce"Zai fi kyau ki sakawa abun albarka kawai kamar yadda na saka, tun da aka yi auren ai dole za ki san wane ne shi, anjima zai zo ya gaishe ki, kuma su gana da ita Sayyadar". Ya kalle ni ya ce"Sayyada kin karɓi auren nan ko na warware shi?" Na sunkuyar da kai na ce"Baba na karɓi zaɓinka da godiya mai tarin yawa, kuma in sha Allah zan yi masa biyayya iya ƙarfina". Baba Ya ce"Idan kika yi haka ni kuma na yafe miki, Allah ka shaida indai Sayyada ta zauna ta da mijinta lafiya ta zama mai biyayya a gare shi na yafe mata duniya da lahira, kuma zan dawwama ina yi mata addu'ar gamawa lafiya da nema mata yafirka, idan ta bijirewa mijinta Allah ka shaida na..." Da sauri na ce"A'a Baba, don Allah kar ka ƙarasa, wallahi na yi alƙarin zan so shi zan yi masa biyayya, ko kuturu ne, ko da bai zo a jinsin ɗan'adam ba na karɓi aurensa, kuma zan zauna da shi lafiya, in sha Allah Baba za ka gamsu da zaman mu, har ka furta ka yafe min". Baba ya sauke ajiyar zuciya ya ce"To Alhamdulillah! Allah Ya sa hakan ya zama alkhairi, kuma mijinki yana sonki, ina kyautata zaton zai yi miki adalci a zamanku har ma ki fara son shi, Allah Ya yi miki albarka". Daga haka ya tashi ya shiga ɗaki, Mama ta bi shi da abinci, ni kuma na shiga ɗaki, na hau gado na fara kuka mara sauti, ko waye wanda Baba ya aura min? Ko zan so shi? Na dai yi alƙawarin zama da shi a duk yadda yake, kuma zan yi masa biyayya da dukkannin zuciyata, sai na ji na ƙagauta daren ya yi ya zo na gan shi. Ana idar da sallar isha'i Baba ya shigo yana ƙwala min kira, na fito, ya ce"Maza kintsa ɗakinku ga mijinki nan zai shigo ku gana, don Allah kar ki ba ni kunya, yana matuƙar ganin girmana". Na ce"In sha Allah Baba ka daina kuka da ni, ba zan ba ka kunya ba, kuma ya shigo kawai ɗaki a gyare yake". Baba Ya ce"Ma sha Allah". Na faɗawa Mama, ta miƙo min babbar sallaya ta ce na je na shimfiɗa masa, na saka hijjabi, na ɗauki sallar na shiga ɗakin na shimfiɗa ta na nemi waje na zauna a takure gabana sai faɗuwa yake yi, ina jiran ganin wane ne mijina? Wata zazzaƙar murya na jiyo tana sallama a tsakar gidan, irin ta cikakkun 'yan ahalus sunna, na zaro ido a raina ina cewa wannan na samu kenan? Ina ji suka gama gaisawa da Mama ta faɗa masa ya shiga ɗakin can, wato inda nake, na sunkuyar da kai sanda ya yi sallama a ƙofar dakin, na amsa ba tare da na ɗago ba, ya shigo ya zauna yana cewa"Ma sha Allah, Alhamdulillah". Fargabar ɗagowa na kalle shi ma na dinga yi, da muryarsa mai kama da ta iyayi ya ce"Assalamu alaiki Ya Sayyada". Na ce"Amin wa'alakassalam, ina wuni?" Ya ce"Lafiya Alhamdulillah, Ya Sayyada yana da kyau ki ɗago ki kalli mijinki, ni ma kuma na kalli matata". Na tsinci kaina da bin umarninsa, na ɗago na kalle shi, sai na ga mutum sanye da jallabiya da hirami, duk da a zaune yake amma na gane yana da tsayi sosai, sannan ba shi da ƙiba siriri ne, fari ne, amma ba kyakkyawa ba, yana ta sakar min murmushi ya ce"Yana da fa'ida ki kalle ni da kyau, kamar yadda ni ma zan so a ce kin cire hijjabin nan, domin na samu damar kallonki da kyau ya ke Assayada". Gabana ya faɗi da jin wai na cire hijjabi, na kau da kai daga kallonsa,ba tare da na cire hijjabin ba. Ya ce"La ba'asa, to Assayada kamar yadda na san mahaifinki ya sanar da ke, ni ma zan sake sanar da ke, ni ce wanda aka ɗaura mana aure a yau, hakan yana nufin a yanzu dai ni ne mijinki bi ma'ana mun zama mallakin juna, Alhamdulillah ina farin ciki da hakan, kuma ina tafa ke ma haka". Na ce"Ina farinciki, Allah Ya ba mu zaman lafiya". Ya ce"Alhamdulillah! Baba ya faɗa min komai game da ke, ni ma kuma akwai abubuwan da ya kamata ki sani game da ni". Ya ɗan yi shiru kafin ya ce"Wato Assayada ni ba cikakken saurayi ba ne, na taɓa yin aure, sai dai watanni uku da auren aka samu matsala ɗalaƙi ya shigo cikin lamarin, bi ma'ana muka rabu da juna, daga nan ban sake aure ba sai kuma yanzu da Allah Ya ƙaddara ke ce matata, Alhamdulillah ina farinciki da hakan". Na yi shiru, ya cigaba da cewa"Akwai wani lamari da ya kamata ki sani game da ni, a gaskiya ina da wata larura, wacce ya kamata a ce na sanarwa da matata lafin auren, to sai shi Baba ya ce babu damuwa ya san za ki amince ki karɓe ni a duk yadda nake". Gabana ya faɗi, na ce"Wace larura ce?" Ya yi murmushi ya ce"Ba wata babba ba ce, wannan larura ita ce, ni dai ban kasance mutum kamar kowa ba, bi ma'ana dai ni hariji ne, wato mai yawan buƙatuwa, amma fa ga iyalinsa, ga halalina kamar dai ke ɗin nan da kika kasance halal ɗina a yanzu, ina da buƙata mara adadi, wanda sai kin zauna da ni za ki fi fahimta, ina fatan hakan ba zai kawo mishkila a zamanmu ba". Jikina ya yi sanyi, ina auna kalmar hariji, ko zan iya? Sai zuciyata ta shiga raya min zan iya, tun da dai Sadam ma ai hariji ne, hmm ashe dai na jahilci kalmar hariji. Na ce"In sha Allah zan iya, Allah Ya ba mu zaman lafiya". Ya ce"To Alhamdulillah, mun yi magana da Baba ya ce wani satin za ki tare, ina da gidana mai ɗaki biyu sai kitchen da banɗaki, yana nan tsaf, sai jiranki kawai da yake yi". Na yi murmushin yaƙe. Ya ce"Assayadda zan so na gan ki ba tare da hijjabi ba, shin hakan zai yiwu ko sai kin tare?" Na ce"Zan so a ce dai na tare ɗin, amma idan umarni ne kake ba ni zan cire". Ya ce"A'a, la ba'asa, ba umarni ba ne, Allah Ya kai mu ranar Juma'ar". Na amsa da amin, ya miƙo min wayarsa ya ce"Yawwa sai ki saka min lambarki a nan ko?" Na zo karɓa, ya riƙe hannuna ram, na kalle shi na ga yana lumshe ido, ya ce"Assayada duk da ba umarni na ba ki ki cire hijjabi ba, amma da kin ce da zan ji daɗi". Na ji kamar na rusa ihu don takaici, ni gaskiya wannan mutumin sam bai yi min ba, amma kuma dole zan zauna da shi na yi masa biyayya ko don Baba ya yafe min, na karɓi wayar na saka masa lambar na ba shi, sannan na zare hijjabin, riga da siket ɗin leshi ne a jikina, kuma ba su kama ni ba, ya fara faɗin "Ma sha Allah, ma sha Allah". Sannan ya ce"Shin za ki yi mini alfarma ki matso daga kusa?" Na haɗiyi wani yawun takaici na muskuta na matsa, ya ce"Ma sha Allah, ya matso yana yi min raɗa a kunne ya ce"Ba ki tambayi sunana ba Assayyada". Na ce"Na manta". Ya ce"Sunana Ashir". Na ce"To". Ya riƙo hannuna ya ce"Na roki wata alfarmar?" Na ce"A'a don Allah ka yi haƙuri, nan gidan iyayena ne, idan muka tare ba ma sai ka nemi alfarma ba". Ya ce"To, to, to, la ba'asa, hakan ma ya yi, to ni zan tafi, domin na ga zaman ba zai haifar da fa'ida ba, sai mun yi waya, zan sake zuwa kafin Juma'ar". Na ce"Na gode, ka gaida gida". Ya fita daga ɗakin, na saka hijjabina, na yi shiru, hawaye ya sakko min. [07/10, 8:18 pm] Sadiya Abdulrazak: LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 15 Tunani na shiga yi, wannan shi ne mijina? Ashe dai ƙaddarata akwai zaman aure da namiji ba ɗaya ba, a baya kafin na auri Sadam gani nake idan ba shi na aura ba har abada ba zan iya zaman aure da wani ba, sai ga shi komai ya canza, yanzu dai ga wanda ƙaddara ta zaɓa min, kuma dole na yi masa biyayya ko da ba na son shi, ko don Baba ya yafe min, yi wa Baba biyayya na zauna da Ashir lafiya ne kawai zai sa ya gane nadamata, don haka zan daure na zauna da shi ko ba na son shi, kasancewarsa hariji kuma ina tunanin babu wata damuwa, tun da Sadam ma haka yake da yawan buƙatuwa, tun da na saba ai kuwa zan jure, na ɗaɗe zaune a ɗakin cikin duniyar tunani, shigowar Mama ne ya sa na dawo daidai, ta zauna tana cewa"Sayyada ki yi haƙuri, don Allah ko ba kya son bawan Allahn nan ki daure ki yi masa biyayya ku zauna lafiya, saɓa masa kuwa kin san zai ɓata ran babanki, kuma zai ɗauka shikenan ba za ki sake yi masa biyayya ba, bai isa da ke ba, kuma burinki na ganin ya yafe miki ma ba zai taɓa cika ba". Na ce"In sha Allah Mama zan zauna da shi lafiya". Ta ce"Allah Ya ba ku zaman lafiya, ga abu ya zo a ƙurace, amma wannan gyara da kika yi na maganin sanyi ai ba na jin ya bar jikinki, duk da haka gobe zan sa a kawo wasu sai ki fara, idan kuma akwai inda kike siyan na gyaran jiki sai ki siya". Na yi shiru kaina a ƙasa, ta ce"A nan za ki kwana ne?" Na girgiza kai alamar a'a. Ta ce"Ya kamata ki tafi gida kin sa tara ta gota". Na tashi na ɗauki wayata na fito, Baba ya ce"Za ki tafi gida ne?" Na ce"E". Ya ce"Yanzu na kaiwa babanki sadakinki yana hannunsa". Na ce"To, sai da safen ku". Na tafi, a gidan na tarar da Anisa, da alama kwana ta zo yi, na yi wa yaranta wasa, ita kuwa kallo ɗaya na yi mata na ɗauke kai, Umma ta ce"Sayyada ashe kuma haka abu ya faru, babanku ya dawo daga masallaci yake faɗa min". Na ce"E wallahi". Ta ce"To Allah Ya sanya alkhairi ya nuna mana ranar tariyar lafiya". Ban amsa ba, na shige ɗaki, Anisa ta biyo ni, babu yabo babu fallasa ta ce"Sayyada amarya, ashe an ɗaura aure". Na ce"Idan Allah Ya nufa duk gulmar algungumi sai dai ko ya haƙura ko ya haɗiyi zuciya ya mutu". Ta ce"Ikon Allah,to kenan wane ne munafuki?" Na ce"Wanda ya tsargu". Kafin ta ba ni amsa kira ya shigo wayata da baƙuwar lamba, haka kawai jikina ya ba ni mijina ne, na ɗauka, na kuwa ji wannan maƙalalliyar muryar tasa ta ustazai yana yi min sallama, don na cusawa Anisa haushi na ce"Wa Alaikassalam mijina". Ya yi murmushi mai sauti ya ce"Alhamdulillah, ma sha Allah! Assayyada na ji daɗi sosai da kika kira ni da mijinki, duk da dai dama haka yake a bisa ƙa'ida, amma da kika furta ɗin sai na ji assurur ya kama ni". Na kalli Anisa da ta kwanta a katifa, na harare ta ta gefen ido na ce"To idan ban kira ka da mijina ba wa zan kira? Yau na fara ganinka, amma sonka ya cika zuciyata babu masaka tsinke, har nake jin anya kuwa ban zaƙe ba?" Da sauri ya ce"La la la, la ba'asa ya Sayyada, sam ba ki zaƙe ba, wannan shi yake nuna ni da ke mun karɓi hukunci Allah kenan, Alhamdulillah, duk da dai ɗazu na yi mamakin yadda ba ki saki jiki da ni ba". Na ce"Haba duk firar da muka yi me kuma kake saka ran zan iya yi maka bayan nan?" Ya ce"Alal haƙiƙa kin saki jiki, amma iya na fatar baki ne, ni a zatona za ki zauna dab da ni mu yi firar fahimta juna, musamman ma da na sanar da ke larura ta, Assayyadda". Na ce"Na'am". Ya ce"Zan so a ce kin yi min tambihi a kan kalmar hariji, domin ina so na san cewa shin da gaske kin gane me kalmar take nufi kuwa?" Na ce"Me yasa kake tunanin ban fahimta ba?" Ya ce"Saboda mata uku na nema aure bayan rabuwa da matata, amma idan na ga dacewar sanar da su ni hariji ne sai su ce ba za su aure ni ba, duk kuwa da irin natija ta, kodayake ba a son yabon kai, sai na yi mamaki da ke kika amince tashin farko, shi yasa na yi zaton ko ba ki san kalmar ba". Na ce"Na sani mana, kuma mijina na baya ma ai haka yake". Ya ce"Allahu akhbar! Alhamdulillah, Alhamdulillah, to a gaskiya ni da ke mun yi dace, mun samu rabo mai girma, domin kuwa Allah ne Ya dube ki ya ba ki ni, domin ba a ce ba ni kika aura ba, akwai yaƙini mai girma na cewar ba za ki iya zaman aure da wanda ba hariji ba, hakan take ni ma a gare ni, idan na auri wacce ba irin halittarmu ɗaya ba, akwai hasashe mai girma a kan cewar za ta cutu, kuma za ta iya tauye mini hakkina idan ba ta ji tsoron azabar Allah ba". Na ce"Uhm!" Don na fara gajiya da zancen harijancin haka, wannan mutumin ban ga alamar yana da kunya ba, yau fa ya san ni kuma daga ganin an ɗaura mana aure sai ya ɓare baki ya dinga sakin wannan maganganun haka? Ya ce"Assayyada" Na ce"Na'am Ya sayyadina". Da wata murya kamar raɗa ya ce"Waccen matar tawa da muka rabu sau biyar nake kiranta a rana, shi ma saboda akwai sauran al'amuran rayuwa ne, shin za ki iya jure hakan?" Wallahi na yi zaton kiran waya yake nufi, don haka na ce"Me zai hana, ni kira biyar ma ai ya yi min kaɗan" Ya ce"Allahu akhbar! Allah shi ne abun godiya, wato dai a bisa dukkan alamu ke ce, bi ma'ana ke ce wacce nake ta roƙon Allah a ƙiyamul laili ya ba ni ke, Alhamdulillah". Na yi yar dariya na ce"Ni ma ina kyautata zaton kai ne". Ya ce"Ƙwarai kuwa". Na ce"Zan kwanta, ina jin bacci sosai". Ya ce"Ma sha Allah, To amma kar ki manta da sallar dare, yanzu kafin ki kwanta yaba da kyau ki yi nafila ki raka'a biyu ce, tana da fa'ida, saboda ko da ba ki samu tashi a tsakiya ko ƙarshen dare ba, bi ma'ana idan bacci ya yi miki nauyi, kin ga da sauƙi tun da kin yi a farkon daren". Na ce"Hakane, na gode da tunatarwa". Ya ce"Hmm zan so a ce kina gefena a yanzu haka, da abubuwa da dama sun faru". Na yi dariya na ce"Sai da safe". Ya ce"Allah Ya tashe mu lafiya". Na ajiye wayar na tashi na kwanta a ƙasan katifar inda yaran Anisa suke kwance, don a nufinta ni da ita mu kwana a katifar, a raina na ce'Kwana nawa ne ma na tafi gidan mijina?' Washegari da safe ya turo min saƙon barka da safiya, da na duba sai na ga ya yi min miss call ƙarfe uku na dare, sai wajen ƙarfe goma ya kira ni, muka gaisa yake cewa"Allah Ya sa dai jiya da na kira ki ba ki ɗauka ba sallah kike yi a daidai lokacin". Na ce"Gaskiya bacci nake, wayar ce a silent shiyasa ban ji ba". Ya ce"Ya subhanallah! Assayyada Allah Ya sa dai ba kya cikin shagalallun da suke raya dare tun farko har ƙarshensa da bacci". Na ce"Ina yin sallah, sai dai idan bacci ya ci ƙarfina". Ya ce"Ma sha Allah! La ba'asa, ai kwanaki ya rage mu zama a tare, ko bacci ya yi miki nauyi kin ga kina da mai tunatar da ke". Na ce"Na gode sosai, zan ji daɗin hakan". Ya ce"La ba'asa, yanzu me kike yi? Ni dai yau da na tashi bayan komawa bacci wajen ƙarfe bakwai saura, sai na yi wanka, na karya da sauran abincin jiya da Inna ta ɗumama, na shirya na tafi kasuwa, yanzu haka ina kasuwa, shin Baba ya sanar da ke maƙota muke a kasuwa?" Na ce"Bai sanar da ni ba, kenan a kasuwa ya sanka?" Ya ce"Ƙwarai kuwa, ya san ni tun da daɗewa, kasancewar ni ne nake jan su sallah, Baba mutumin kirki ne mai dattako, Allah Ya saka masa da alkhairi". Na ce"Amin Ya Allah". Ganin zai sake kwaso zance na ce"Bari na je na yi aikin gida". Ya ce"Na'am, la ba'asa, anjima za mu yi waya, amma ki yi haƙuri ba zan zo ba, saboda jiya bayan komawa ta gida na shiga wani yanayi, ke kuma na ga kamar idan na so ki ɗan rage min kewa ba za ki iya ba, duba da ganin yadda jiya kika saka hijjabi". Na ce"E gaskiya ba zan iya ba, tun da kwanakin babu yawa, kamata ya yi mu yi haƙuri har mu tare". Ya ce"To la ba'asa Ya Assayyada, Allah Ya ƙara mana haƙuri bakiɗaya". Na amsa da Amin, muka ajiye wayar. A ranar Mama ta kira ni da yamma, ta ba ni maganin sanyi da na ƙarin ni'ima ingantattu, na duƙufa sha ina amfani da su, kullum Malam Ashir zai kira ni sau biyu a rana, safe da dare, mun saba da shi babu laifi, kullum sai ya kira ni da daddare ƙarfe uku, idan na ɗaga sai ya ce na tashi na yi sallah, sai na tashi ɗin. Ana gobe zan tare aka je aka yi jeren kayana, a ranar kuma ya zo ya tambaye ni babu wata walima da zan yi? Na ce babu, iyayena mata dai za su yi wuni a aranar don mutane su shaida auren, ya ce"Ma sha Allah, idan na fahimta daidai kenan hakan yana nufin ba kya buƙatar komai dangane da ɗan kuɗi haka ko?" Na ce"Ba na buƙatar komai". Ya ce"To Alhamdulillah! Sai dai Allah Ya sa dai akwai 'yan kyawawan suturu da za ki dinga ado da su, dayake Baba ya ce ba sai na yi lefe ba, dubu ɗari kawai yake buƙata a matsayin sadaki, amma bisa adalcina in sha Allah bayan kin tare zan yi miki abin da ya sawwaƙa". Na ce"Na gode sosai". Ya ce"Alhamdulillah, yana da fa'ida ki san ita rayuwar duniya hudusun ce kuma fana'un, lahirarmu ya kamata mu gina ba ƙyale-ƙyalen duniya ba". Na ce"Allah Ya sa mu dace". Ya amsa da amin. Daga nan muka taɓa fira, ya tafi. Washegari aka yi wuni a gidanmu, ni dai babu wanda na gayyata, amma wasu daga cikin ƙawaye da suka kasance 'yan'uwa sun zo, na san duk Anisa ce ta gayyace su, bayan magriba Babana ya aiko na je, na je ya zaunar da ni ya dinga yi min nasiha, da faɗin kar ya ji wata ɓaraka daga wajena, ya yarda da Malam Ashir yana da tabbacin za mu zauna lafiya Indai ba ni ce na tsiro da fitina ba, zaren neman yafiyata na sarƙafe da wannan auren, idan na ja shi sannu a hankali zai yafe min, idan na ja shi da ƙarfi ya tsinke na huta, na dinga kuka ina faɗa masa zan yi biyayya da dukkan ƙarfina, Mama ma ta yi min nasiha da fatan alkhairi, a gidan na zauna bayan sallar isha'i malam Ashir ya zo da babur ɗinsa ya ɗauke ni, haka na ɗare bayan babur babu ɗan rakira, na ja hujjabina na rufe rabin fuskata, tun da muka fara tafiya wata kalma ba ta haɗa mu ba, sai tasbihi yake yi da hamdala, har muka ƙarasa ƙofar ƙaramin gidan nasa, ya tsaya yana cewa"Alhamdulillah, amaryata mun iso gidanki". Na sauka daga babu ɗin, ya saka mukulli ya buɗe gidan, ya shigar da babur, na bi bayansa, ya faka shi daga gefe, ya koma ya saka sakata, ya zo yana ta hamdala ya buɗe ƙofar ɗakin duka biyu, ya ce"Bisimillah Assayyada, udkul bis salam". Na yi bisimillah na saka ƙafata a cikin ɗakin, falo ne, na zauna a kujera gabana yana faɗuwa, jikina duk ya mutu, ya yi sallama ya shigo yana ta aikin murmushi, da leda a hannunsa, ni dai lokacin da ya ɗakko ni ban ganta ba, shi yasa na fi zaton yanzu ya ɗakko ta daga ɗakin gadon, ya ajiye ledar yana cewa "Assayyada yana da kyau mu fara gabatar da Sallah kafin komai, domin mu nuna godiya ga Allah da Ya sanya mu cikin zaɓaɓɓu cikin bayi wanda ya huwace mana mu keɓe kanmu mu raya sunna, domin mu hayayayyafa Manzon Allah Sallallahu alaihi Wa sallama ya yi alfahari da mu ranar gobe ƙiyama". A raina na raya wannan mutumin ba dai surutu ba, yanzu faɗin tashi mu yi sallah ne ya kwaso dogon zancen nan? Na amsa da to, sannan na tashi, na yi alwala shi ma ya yi, ya ja mu sallah a falon, bayan mun idar ya dinga kwararo mana addu'ar neman albarka a cikin aurenmu, sannan ya dafa kaina ya yi min addu'a, ya ce"Assayyada a gurguje ga leda nan sai ki ɗauka ki buɗa ki ware kaza da lemo, sauran kuma abun karin kumallo ne, wanda za mu sarrafa shi da safe idan Allah ya sa muna cikin rayayyu kuma lafiyayyu". Na ce"To". Na ɗauki ledar na buɗe, na fito da kazar sai lemo coca cola jarka biyu, sauran kuma suga ne wanda ba zai wuce ƙullin naira ɗari ba, sai madara yar ta leda guda ɗaya da milo shi ma guda ɗaya, sai ganyen shayi guda ɗaya, wannan dai me guda biyu a cikinsa ɗin, sai wani matsolon biredi, wanda indai da iya shi kaɗai zan karya babu ƙwai ko indomi ba lallai na ƙoshi ba, ɗan ɗari uku ne, ɗari ukun zamanin Tunubu ba ta da ba, abun ya ba ni mamaki, amma na yi ƙoƙarin shanye mamakina, na tashi na kai kayan shayin kitchen, na adana, sannan na ɗauki faranti da kofina biyu, zan juye kazar ya karɓa yana murmushi ya ce"Yana da fa'ida a ce miji yana taya matarsa hidimar gida, ya juye ƙedararriyar kazar, daga gani 'yar Hausa ce ba wata babba ba, a raina na ce'Allah ga Sayyada'. Ya rage kayan jikinsa ya zama daga shi sai singlet da boxer, sai yanzu na kara ganin ramar shi, kunya duk ta kama ni, ya ce"Amaryata ko da ba za ki rage kayan jikinki yanzu ba, zan so a ce kin zo kin zauna a nan cinyata". Na ji kamar ba zan iya ba, da jikin Sadam kawai na saba, yau ga ƙaddara ta saka zan raɓi wannan busasshen mutumi, na ce"Umarni ne?" Ya ce"Ƙwarai kuwa, a yanzu a ƙarƙashin ikona kike, duk wani abu da zan faɗa miki umarni ne, musamman ma a wannan dare mai albarka, haka na tashi na ajiye mayafina, na je na yi yadda yake so, yana cin kazar yana ba ni a baki, kaɗan na ci na ce na ƙoshi, na tashi na fita, ɗayan ɗakin na shiga na rage kayan jikinana fito na shiga wanka, na fito na same shi ɗaure da wani tsohon towel, amma fes yake babu ƙazanta, ya yi min murmushi ya ce"Hana habibiya, inda kin faɗa min za ki shiga wanka ne ai da mun shiga a tare ko? Cikin hakan akwai fa'ida". Na yi murmushin yaƙe na ce"Gobe sai mu yi". Da sauri ya ce"In sha Allah". Ya zuba ruwan shi ma ya yi, lokacin da ya shigo ɗakin na saka rigar bacci har na kwanta, tunani kawai nake yi, a yadda wannan mutumin yake rawar kai yana kiran kansa da sunan hariji yau ba zai saurara mini ba, hawaye ya siraro gefen idona, wai ina ji ina gani da yardata a yau wani ba Saddam ba zai shiga hurumina, rayuwa kenan. Malam Ashir ya gama komai ya hayo gadon, tun kafin ya kai hannunsa jikina na ji yana karanto addu'ar saduwa da iyali, hakan ya ƙara bugun zuciyata. Tun a ranar na fara zargin anya kuwa Sadam hariji ne? Domin a ya daɗe ya yi minti talatin, duk ranar da ya yi awa ɗaya to zarginsa nake na ce akwai abin da ya sha, kuma sosai yake tara min gajiya, amma wannan mutumin idan na lissafa daidai yanzu haka dai idan bai yi awa uku ba to ya yi biyu da rabi, na gaji duk kuwa da gyaran jikin da na yi, tun da nake da Sadam bai taɓa irin wannan daɗewar ba, ko sanda nake buduruwa ne kafin aurenmu, tun ina daurewa har na gajiya, da muryar kuka na ce"Malam bai isa ba ne?" Yadda kuka san fa kurma nake magana, bai ma nuna ya ji ba sambatu kawai yake yi ya yi Hausa ya yi larabci, da na ga da gaske ba zai saurare ni ba na ture shi da ƙarfi ina faɗin"Na gaji fa!" Na sauke numfashin da nake jin kamar ya kusa ya fara min nisa. Wallahi bai turo ba, kamar wanda aka maƙale jikinmu da gum, amma a wannan karon ya saurara ya ce"Subhanallah! Haka ya ke Assayyada, shin kin san ɗumbin ladan dake ɗanfare da wannan ibada kuwa? Ba ki san cewa ana sakawa a rai tamkar mutum ya shiga filin yaƙi ba ne yana kashe arna? Kin san dai yaƙi da arna jahadi ne babba ko? Daure ya ke matata mu ƙarasa raya wannan dare mai albarka da tarihi a gare mu". Na ce"Na gaji sosai, don Allah ka rabu da ni haka a bar wa gobe komai". Ya ce"La ba'asa, amma dai... Kodayake na yi miki uzuri tun da akwai gajiyar taro a tare da ke, na yafe miki". Ya matsa gefe yana cewa"Sannu, na gode sosai Assayada, da asuba ma ƙarasa idan kin huta". So na yi na yi bacci a yadda nake ɗin, amma ya yi min dole na je na yi wanka, na kwanta bacci ya ɗauke ni, don ban ma ji fitowarsa daga wanka ba. Na yi mamakin ganin yana sallar dare da na farka, na kuma ji daɗi da bai tashe ni ba, saboda har ga Allah ba zan iya ba, ƙarfina ya kusa ƙarewa, da asuba ya tashe ni na yi sallah, kafin ya dawo daga masallaci na koma gado bacci ya fara fizga ta, sautin muryarsa ne ya wartsakar da ni kamar munafuki yake cewa"Assayyada kin huta mu ƙarasa yaƙin? Babu fa'idar barin arnan nan fa". 08028066015 [08/10, 4:40 pm] Sadiya Abdulrazak: LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, KU YI MIN ADALCI KU BIYA NI HAKKINA. 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 16 Gabana ya faɗi da jin furucinsa, ni fa a yadda nake jin kaina nan da jibi ma ba zai samu ba, ya rage kayan jikinsa ya hau gadon yana cewa"Assayyada kin huta?" Kamar zan yi kuka na ce"A'a". Ya janyo ni jikinsa yana cewa"Haba, haba Assayyadata, ni fa jiya ma kin ba ni mamaki, har na fara tunanin anya kuwa irin larurarmu ɗaya? Ki ka ce ke ma..." Bai ƙarasa ba na ce"Ni ba harija ba ce, ban san abin naka ya yi tsanani haka, don Allah ka tausaya min". Ya ce"Subhanallah!". Sai ya yi shiru na ɗan lokaci, kafin ya ce"To yanzu dai tun da ba kya so ba zan matsa miki ba, idan don ta ni ne ki bar ni a wahale, to amma sai dai wannan laifi ba ni kika yi wa, da Allah kike, bi ma'ana yanzu za ki shiga sahun matan da mala'ikun Allah za su dinga tsine musu, ba za su gushe suna tsine miki ba har sai lokacin da na aminta da ke, bi ma'ana na yafe miki". Na ji ya kashe min jiki da wannan wa'azin, na san shi tun muna islamiyya, amma ina tuna wahalar da na sha daren jira, sannan idan zai yi min adalci ai bai kamata ya yi fushi da ni ba. Ya yi gyaran murya ya ce"Assayyada shin za ki iya jure tsinuwar mala'iku? Yau ko wani bawan Allah ne ko wani malami ya saka sunanki a gaba yana tsinewa ya za ki ji? Ballantana kuma a ce mala'iku wanda ba sa saɓawa Allah sai bautarsa, wa iyazubillah! Sayyada ki duba lamarin". Na fara hawaye na ce"Don Allah ka yafe min to, ka aminta da ni, da daddare zan ba ka in sha Allah!". Ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Subhanallah! Assayyada da dai za ki taimaka ɗin, kin ga jiya ma daga ƙarshe kamar korata kika yi, sai dai na dubi Allah na yafe miki, tausaya ni ma ki yi min adalci mana" Na ce"To shikenan". Haka ya ɗora daga inda ya tsaya, ina ta hawaye, sai da gari ya waye tangararan, shi ma ga ni ya yi sautin kukan nawa yana ƙaruwa ne, ya ƙyale ni, amma duk wannan sadaukarwa da na yi masa sai cewa ya ce"La ba'asa Ya Assayyada, amma dai ki shirya kafin na dawo daga kasuwa". A raina na ce'ba sai ka same ni a ɗakin naka ba?' A fili kuma ko kallonsa ban yi ba, na kasa tashi, har ya yi wanka ya fito, ya ce"Na lura kamar jikinki babu ƙwari ko? Bari na dafa mana shayin". Ban kula shi ba, saboda lokaci ɗaya na fara jin haushinsa, ya shiga kitchen, ya kunna gas don a cike aka kawo shi gidan, ya dafo shayin, a falo ya karya, sannan ya shirya zai tafi kasuwa duk ina kwance, ya shigo ɗakin ya zauna ya fara yi mini nasiha a kan zama da janaba, ya ɗora da faɗin"Da kin san matsalolin zama da janaba da ko da rarrafe kin shiga banɗaki kin yi wanka". Na ce"Na ji, zan tashi". Ya ce"La ba'asa, bari na tafi kasuwa, ga abincinki can a falo, wajen sha biyu haka zan dawo gidan, zan kawo miki abin da za a dafa da rana". Na ce"To a dawo lafiya". Ya tsaya yana kallona ,irin kallon nan mai cike da sha'awa, na kau da kai ina ɓata rai, ya sauke numfashi ya ce"La ba'asa, amma yana da kyau mu zauna da ke mu yi karatun muhimmancin ba wa miji cikakken hakkinsa". Na ce"Au yanzu ban gamsar da kai ba kenan?" Ya ce"La la la la, ni ban ce ba, kin dai yi iya yinki amma akwai gyara a lamarinki Assayada". Ya fita daga ɗakin yana cewa"Sai na dawo, don Allah ki tashi ki samu tsarki". Na sake cewa"A dawo lafiya". Na tashi bayan ya fita, na saka sakata a ƙofar gidan, na shiga banɗaki na yi wanka, sannan na yi na sabulu ma, na fito na shirya, na shiga falo, cikin ƙaramin kofi mai murfi na hangi shayin nawa a can ƙasan kofi, ga kuma guntun biredin da ya rage min, shayin ma har ya yi sanyi, kuma ba zan ƙoshi ba, takaici ya kama ni ban san sanda na fashe da kuka ba, na tuna gidan Sadam, komai na abinci ga shi nan danƙam a store, sai wanda na ga dama da shi zan karya, na haɗa shayi mai matuƙar kauri, yau ga ni a gidan aurena da abu a gabana kamar an ci an ragewa almajira, yunwa nake ji, don haka na ci, na shiga kitchen na ga farantin sauran kazar jiya, ashe bai cinye ba, na ɗauka na cinye, na gyara gidan na kwanta, tunawa da na yi ba lallai ya ƙyale ni ba yau ma, ga kuma wajen nan ya ɗaure min duk babu daɗi, na dafa ruwan zafi na shiga na zauna, na ɗan ji daɗi a jikina, na kwanta bacci ya ɗauke ni, bugun gida ne ya tashe ni, na je na buɗe idona cike da bacci, shi ɗin ne ya dawo da leda a hannunsa, ya shigo da babur ɗin, yana cewa"Ya subhanah! Haba Assayyadata ban yi zaton haka daga gare ki ba". Na ce"Me na yi?" Ya ce"Ta ya za ki zo ki buɗe ƙofa kai tsaye ba tare da kin san ko wane ne ba? Ai ya kamata ki fara saka hijjabi yadda ko an samu matsala wani bai ga jikinki ba". Na ce"Yi haƙuri, zan dinga sakawa". Ya yi murmushi ya ce"Ko ke fa". Na ce"Sannu da zuwa". Ya ce"Yawwa". Muka shiga falon, ya ce ga wannan sai a dafa ko, amma kafin nan, zan so a ce kin taimake ni, bi ma'ana mu ɗan keɓe ko na 'yan mintuna ne". Gabana ya faɗi na ce"Mu keɓe kuma? Ka manta ka yi fa safen nan?" Ya ce"Ban manta ba, ai a baya na faɗa miki nakan yi kira a ƙalla sau biyar ne a rana, shi ma fa saboda al'amuran rayuwa ne, tun da dai ai ba don shi kaɗai aka halicce mu ba". Ya tashi ya dawo kusa da ni yana naniƙata, da muryar kuka na ce"Don Allah ka yi haƙuri, gaskiya na gaji, ba zan iya ba". Ya ce"Subhanallah! Ya Allah ina nemawa matata Assayyada yafiyarka, Allah na yafe mata, ban yi fushi da ita ba". Na fara shassheƙar kuka, ya marairaice ya ce"Don Allah ki tausaya min, na kasa zaman kasuwar, ni azabar Allah ma na fi jiye miki, ba halin da zan shiga ba". Na ce"To, amma don Allah ka dinga yi min adalci, idan aka cigaba da tafiya a haka zan cutu". Ya ce"Za ki saba in sha Allah, Allah Ya yi miki albarka". Da Allah Ya taimake ni yanzu dai bai wuce minti ashirin ba, na yakice shi da ƙyar, ƙafafuna har harɗewa suke yi, jikina duka ciwo don ma dai ba shi da ƙiba, na yi wanka, na shiga kitchen don ɗora girki, amma na kasa komai na zauna na fara kuka. Ya shigo bayan ya yi wanka ya ce"Subhanallah! Assayyada lafiya? Mene ne ya saka ki kuka?" Na share hawayen na ce"Babu komai". Na janyo ledar ina cewa"Me zan dafa?" Ya ce"Ki yi macaroni da miya, akwai sauran kazar jiya sai ki saka a cikin miyar". Ban kula shi ba saboda takaici, ya ce"Hanzarta, na ci na koma kasuwa". Ya koma ɗaki ya kwanta bacci ya ɗauke shi. Na dafa macaronin leda ɗaya da miyar jajjage, na zuba na zauna na ci a kitchen ɗin, na sha ruwa, sai yanzu na ƙoshi tun da na zo gidan, na zuba na shi a faranti na zuba ruwa a kofi na kai masa, na same shi yana bacci, a raina na ce'Ai dole ka yi bacci mana, jarababbe kawai'. Kamar na tashe shi, sai kuma na rabu da shi, na zauna ina ɓata rai, sai ga shi ringing ɗin wayarsa ya tashe shi, ya tashi a firgice yana cewa"Subhanallah" Sannan ya karanto addu'a tashi daga bacci, ya ɗauki wayar yana cewa ga shi nan zuwa, yana gamawa ya kalle ni ya ce"Assayyada me ya hana ki tashe ni? Zan koma kasuwa fa" Na ce"Ai na san kana buƙatar baccin shiyasa". Ya ce"Ai akwai lamuran da suka fi baccin a daidai wannan lokacin". Ban ce komai ba, ya fita ya kuskure baki, ya dawo, ya ja abincin, ya ce"Bisimillah, matso mu ci". Na ce"Na ci nawa". Ya ce"To kuma kin ci naki kika ciko min faranti har haka? Wannan ai ya yi min yawa". Ban ce komai ba, ya fara cin abincin ya ce"Ina sauran kaza da na ba da umarnin ki sanya ta a cikin miyar?" Na ce"Ni fa ba cinye tun da safe, saboda wannan ɗan shayin sam ban ƙoshi ba". Ya ce"La ba'asa, dama ba zuba shayin kaɗan ne don sugan ya ba da ɗanɗanon da ake so, amma idan kina ganin za ki iya sha ko da zaƙin nasa ya yi rauni kin ga idan Allah Ya sa gobe muna cikin rayayyu kuma lafiyayyu bayan an gama haɗawa sai ki ƙara ruwa a naki". Takaici ya hana ni cewa komai, ya gama zai fita na ce"Me za a dafa da daddare?" Ya ce"Subhanallah, kina nufin yanzu nan macaroni leda ɗaya ce muka cinye?" Na ce"Saura yar kaɗan dai, ko ni kaɗai ba isa ta za ta yi ba, zan ma iya cinye ta da yamma". Ya ce"Subhanallah, Assayyada akwai buƙatar a yi miki tuni kan wata aya da Allah subhanahu Wa ta'ala Yana cewa "Kada ku yi almubazzaranci, lallai masu almubazzaranci su 'yan'uwan shaiɗanu ne, Assayyada kada daɗin duniya ya saka ki shagala ki manta wannan ayar, kuma shi kansa cin abinci barkatai ba shi da wani amfani, illa ne ma ga lafiya, Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce a raba ciki gida uku, kashi ɗaya abinci, kashi ɗaya ruwa, kashi ɗaya iska, idan kika cike duka cikinki kin kaucewa faɗin ma'aiki, Ya ke Assayyada haƙiƙa ina da zama da ke, yanzu sauri nake yi, bari na dawo za mu yi magana, ita rayuwa ba haka take ba". Na ce"To yanzu dai me za a dafa". Ya ce"Kar ki sake ɗora tukunya, wacce ta rage ɗin ki ci, idan ya so ni zan taho da wani abun sai na ci". A sanyaye na ce"A dawo lafiya". Bayan fitarsa na zuba tagumi, na kalli farantin da ya ce abinci ya yi masa yawa, kuma ga shi ya cinye shi tass, hakan na nufin dai noƙe cikinsa yake yi ba don ya ƙoshi ba kenan, ni Sayyada wa na aura? Wace rayuwa na shigo haka? Na yi wanke-wanke, na yi sallar azhar, na kwanta bacci ya ƙara ɗaukata, wannan bacci nawa har da gajiyar da ya tara min, ana kiran sallar la'asar na tashi, cikina wayam kamar an yashe abincin da na ci, dama indai na yi baccin rana haka nake tashi da matsananciyar yunwa, da a gidan Sadam ne sai na sha Cornflakes, golden morn, Cerelac, snacks, yogurt, ko na haɗa shayi na sha, ba na ma rabuwa da manyan biscute kala-kala, idan ta raya min sai na yi alawar madara na yi ta sha, to yau ga ni a gidan da ko garin kwaki ba a ajiye ba, madara leda ɗaya mu biyu, Ya Allah. Duk yadda na so na na danne zuciyata kar na ƙi cin macaronin nan sai da na cinye shi, saboda yunwa nake ji, har ga Allah ba zan iya kaiwa dare ban ci abinci ba, wajen magriba zuciya ta dinga raya min na dafa taliya na ci na ƙoshi na maze, amma dai na haƙura, ina tunanin tun da ya ce zai shigo da wani abun ƙila irin kazar jiya ce, ma ci tare. Na ɗauki waya na kira Mama muka gaisa, ta ce gobe za a kawo min gara, Baba ya haɗo min kayan gara, ita kuma yau ɗin dubulan da cincin take yi min shi yasa ba a kawo ba, gobe za a haɗa a kawo". Na ji daɗi sosai, na yi mata godiya, ta ce"Sayyada kina lafiya ba wata matsalar dai ko?" Na ce"Lafiya lau Mama". Ta ce"Don Allah ki kwantar da hankalinki, ki riƙe aurenki Sayyada, yaron yana sonki tun da har bai damu da abin da kika aikata ba, yanzu da kin fito za a ce ba kya zaman aure". Na ce"Zan zauna in sha Allah Mama, Ku taya ni da addu'a Allah Ya ba ni ikon jurewa". Ta ce"Kenan akwai matsala?" Na ce"A'a, kawai dai ban fara jin son shi ba ne har yanzu". Ta ce"Ai yanzu aka fara zaman Sayyada, indai kin buɗe zuciyarki za ki so shi, babanki ya ce mutumin kirki ne". Bayan mun gama wayar, na kira Baba muka gaisa na yi masa godiyar gara, ina jinjina lallai Baba yana son wannan auren nawa, tun da wancen bai yi min ba. Na kira Babansu Anisa muka gaisa, na kira Umma ma, ina idar da sallar magriba ya dawo gidan, ya zauna na yi masa sannu da zuwa, na ce"A kai maka ruwan wanka?" Ya ce"E kai min, ba don ina gudun shigar lokaci ba ma ai da kin taimake ni kafin wankan". Ban kula shi ba don na fara tunanin cire shi daga cikin mutane, idan ba doki ba wane ne zai yi wannan aikin? Na zuba ruwan na kai, da ya fito shiga wankan sai da ya riƙe ni a tsakar gidan ya tattaɓa ni, da ƙyar na samu ya tafi wankan, bayan ya fito ya zauna yana karanta Qur'ani da ƙira'a mai daɗi har lokacin isha'in ya yi, ya tashi yana cewa"Bari na je lokaci saura kaɗan, ni nake Limancin sallar isha'i". Na ce"A dawo lafiya". Ana idar da sallar ya dawo, da leda a hannunsa, wallahi na yi zaton kazar ce ko balangu haka, ya ce na ɗakko masa faranti, na ɗakko a raina ina raya yau ba zan yi irin na jiya ba na bar masa kazar nan, sai na ma fi shi ci wallahi. Yana juyewa kawai na ga ashe gurasa ce, itan ma yar kaɗan, sai tilin kabeji da albasa, raina ya ɓaci, ya kalle Ni ya ce"Assayyada ki kawo wannan macaronin sai mu haɗa mu ci bakiɗaya". Na ce"Ni fa na cinye shi". Ya ce"Subhanallah kin cinye? Ina fatan dai kin ƙoshi ko? Bi ma'ana yanzu gurasar nan sai dai ki ci don marmari". Na ce"Wallahi yanzu ma yunwa nake ji, ni fa macaroni ba ya ma ƙosar da ni sai dai kawai na ci". Ya ce"Subhanallah, lallai akwai matsala, haƙiƙa macaroni ya haramta a gidan nan, nan gaba ba zan sake siyo shi ba, duk abin da ba zai ƙosar ba mene ne amfaninsa?" Na ce"Sai a ci don marmari". Ya yi murmushi ya cd"Assayyada kenan, yanzu dai matso mu ci wannan ɗin, duk da ba ta da yawa, amma idan mun yi hakan ma sunna ne". Na ce"Ban gane ba". Ya ce"Nana Aisha ta ce manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama bai taɓa cin gurasa ya ƙoshi ba, don haka mu ma kin ga ya kamata mu ci ta don marmari ko". Na ce"Hakane". Yana ci yana ba ni a baki, sai wasu abubuwa yake yi min masu kama da tausa, har muka gama, muka yi brush, ya tafi ɗakin gado, ni kuwa ina sane na yi zamana a falon. Can sai ga shi ya biyo ni yana cewa"Haba Assayyadata ya ga aikin lada kuma za ki ware kanki ki yi zaune a falo?" Kamar zan yi kuka na ce"Ba na jin bacci ne, zan taho". Ya ce"Dama ba bacci zan yi ba ni ma, taimaka mini za ki yi, daure kin ji habibiyata". Ya kamo hannuna, yana cewa"Ni tsinuwar mala'iku nake jiye miki, in don ta ni ne zan iya yafewa". Yau ma haka ya tisa ni a gaba kamar abinci, sai da na fara yi masa kuka sosai sannan ya sarara min yana cewa ya yafe min, amma bai ƙoshi ba, ban iya bacci ba sai da na shiga ruwan zafi, wani wahalallen bacci ya ɗauke ni wajen sha ɗaya da rabi, ƙarfe uku ya tashe ni, haka ya ja mu jam'in sallah muka yi addu'o'i, sannan muka koma bacci, yau ma da asuba da ya dawo sai da ya ƙara tisa ni a gaba, da safe ya fita ya siyo indomi guda uku, ya miƙo min yana cewa"Wannan ɗaya da rabi za ki dafa mana mu karya, bi ma'ana ta kwana biyu ce, ga suga nan, amma babu madara tun da zai kasance ne tamkar sinadari, kasancewar ba da biredi za a ci ba". Ya shiga ɗaki ya bar ni riƙe da ledar da sakakken baki, indomi ɗaya ce take ƙosar da ni, tsakani da Allah, idan tare da Sadam ne uku nake dafawa, yanzu shi wannan wayo ne ko cutar da kai? 08028966015 [09/10, 6:07 pm] Sadiya Abdulrazak: LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, KU YI MIN ADALCI KU BIYA NI HAKKINA. 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 17 Na shiga kitchen ɗin, na dafa kamar yadda ya ce ɗin, na tafasa shayin, na kai falo, na tarar da shi zaune a kujera yana gyangyaɗi, na tsinci kaina da hararar shi, ina sane na buga cokaci a jikin farantin ya ɗan yi ƙara, sai kuwa ya farka firgigit, yana shafa fuska ya ce"Yi haƙuri ashe bacci ya ɗauke ni". Na ce"To ai dole ka yi bacci, ka raba dare kana abu ɗaya, sannan ka sake katse bacci ka yi sallah, kuma ba samun space ɗin baccin rana kake ba, abun ya maka yawa". Ya ce"Hakane, amma ai duk sun zama dole ne, babu wanda za a rage a cikinsu, farkon dare a bawa gangar jiki hakkinsa, ƙarshen dare kuma a nemi lahira, kin san na ɗan jima babu auren, na saba yin bacci a farkon dare, yanzu kuma abubuwa sun samu, shiyasa dole bacci ya dinga gizgata kafin jikin ya saba". Na yi shiru ban ba shi amsa ba, na zuba masa shayin a kofi, na juye duka sugan, ya ce"Subhanallah, ya za ki zabga wannan uban suga har haka?" Na ce"Ka sha ka ji idan ya yi yawa". Ya ce"Ba lallai ya yi yawa ba, amma ke fa?" Na ce"To wannan manejin na mene ne? A ce suga ma ba za a siyo wanda zai isa ba?" Ya tsaya yana kallona na 'yan sakanni, kafin ya fara girgiza kai kamar wanda ya ji maganar da ta ba shi mamaki ko tsoro, ya ce"Kaico! Kaiconki Ya ke Assayyada, shin kin manta ni mijinki ne? Kin manta a ƙarƙashin ƙafata za ki samu aljanarki?" Tsoro ya kama ni na ce"To yanzu me na faɗa me zafi a nan wanda zan iya rasa aljannata?" Ya ce"Ba ga shi kina neman ja da ni ba, tun jiya nake jera doka kina bi ta kai kina tattakewa, tun da na ce ga yadda lamarin gidan zai kasance ai ke na ki kawai sam'u wa ɗa'a, wannan abubuwan da kike yi ba halin macen ƙwarai ba ne, don Allah ki gyara tun yanzu". Na ce"In sha Allah!" Ya raba shayin gida biyu, ya ɗauki fulas ɗin ya ƙara zubawa, zai zuba a ɗayan na ɗauka na ce"Ni ka bar min a haka, ko kurɓa uku ne gara na yi a kan na sha babu zaƙi". Ya ce"La ba'asa, amma dai Assayyada ya kamata ki rage buri, rayuwar duniyar nan ba komai ba ce". A tare muka fara cin indomin, sai da ta rage saura cokali biyu ya tashi ya bar min yana hamdala, ya ce"Ma sha Allah! Idan har kana bin ƙa'idar cik abinci za a same ka lafiyayye ta kowane fanni, don haka yana da kyau a rage ci, ba shi da wani amfani". Na ce"Me za a dafa da rana?" Ya ce"Ai akwai kayan miya ko?" Na ce"E". Ya ce"To ina ga ki dafa shinkafa, duk yadda kika yi ko jollof ko da miya". Na ce"To a dawo lafiya". Har ya tafi ya dawo ya ce"Aff, ba mu yanke adadin dafawar ba, ai ina ga gwangwani uku za ta ishe mu daga rana zuwa dare ko". Na yi jim, kafin na ce"Anya kuwa?" Ya ce"Za ta isa mana, haba Assayyada, na fa yi zaman auren nan, kuma waccen matar haka take dafawa, Alhamdulillah tana isa a ci, na faɗa miki fa ki koyi raba cikinki gida uku, a sha ruwa a bar kuma iska, gobe Litinin ma ai ranar azumi ce". Na ce"Amma fa zan yi baƙi yau ɗin, kuma ban san su nawa ba ne". Ya ce"E to, wannan yana da kyau ka tarbi baƙinka, sai ki dafa musu taliya ko macaroni leda ɗaya, kin ga sai ta fi daɗin lissafi, mu shinkafar su taliya ko macaroni". Na ce"To, a dawo lafiya". Ya ce"Allah Ya sa". Na shiga gyaran gidan, na gama na yi wanka na kwanta, na shiga tunanin wannan mijin nawa yana so na ko kuma kawai ya aure ni ne don ya dinga samun wajen sauke buƙatarsa? Ni dai har yanzu ban ji ya zaunar da ni ya ce ya fara sona ba, ko ya tambaye ni ina son shi ko akasin haka, amma dai zan zuba masa ido na ga gudun ruwansa, ni dai har yanzu ba na son shi, kuma ba na jin zan so shi wallahi, sannan idan na yi iya dauriyata na gaji dole mu zauna da shi a kan wannan larurar tashi, ko ya koyi zuge tazugensa, ko kuma ya sake ni ya nemi daidai da shi, domin shi ba sa'an aurena ba ne. Wata zuciyar ta ce min anya Baba zai yarda ya karɓi uzurinki? Na ƙarfafi kaina da faɗin zai yarda in sha Allah. Tun jiya babu wuta, wayata ta kusa mutuwa babu caji, ga shi ina son yi chatting ko kallo don ɗebe kewa babu dama, kewar gidan Sadam ta kama ni, ta dinga nuƙurƙusata, a can idan cajina ya kare to ni na so, muna da sola babba, ga kuma generator, na fara tunanin anya ban yi kuskure ba kuwa? Me ma Sadam yake yi min da ya sa na kasa yafe masa? Zuciya ta shiga tunasar da ni shi ne wanda ya lalata miki rayuwa, ya sa mahaifinki yake fushi da ke, ya ɓata miki suna a gari har kika kasa auruwa, sannan ya tauye ki ya hana ki haihuwa, a ƙarshe ya karya alƙawarin da ya yi miki na cewar ba zai yi miki kishiya ba, nan take na ji ina kan daidai, Sadam mugu ne ya cuce ni, don haka babu sauran amfanin zama da shi. Haka na yi ta saƙa da warwara kafin bacci ya ɗauke ni, wajen sha ɗaya na tashi da yunwa, kamar ban karya ba, tsakani da Allah ji na yi ba zan iya jiran dahuwar shinkafa ba, don haka na dafa indomi guda na cinye na sha ruwa, sannan na ɗora ruwan shinkafar, tsakani da Allah ba zan dafa gwangwani uku ba, huɗu na saka, tun da shinkafar za ta kai kwano biyu ya siyo, ba lallai ya gane ba, na ɗumama miyar jiya. Wajen ƙarfe ɗaya ta dawo, na yi masa sannu da zuwa, ya amsa yana murmushi, ya ce"Sannu da gida Assayyada, ya ƙoƙari ya zaman kaɗaici?" Na ce"Alhamdulillah, ya kasuwa?" Ya ce"Mun gode Allah". Na ce"A kawo maka abincin?" Ya ce"Kafin abincin dai da an yi yaƙin nan, samun lada ai ya fi abinci ko?" Ya yi maganar yana bi na da kallon da ko bai faɗa ba na san me yake nufi. Na ɓata rai na ce"Don Allah ka yi haƙuri, wallahi na fara gajiya". Ya ce"Subhanallah!" Yana girgiza kai kamar abun tausayi ya ce"Da ladan kika gaji? To a gaskiya ko da a ce kin gaji da gasken, gajiya ba hujja ba ce, aure ibada ce, wannan wannan lamarin shi ne auren, daure ki dinga ba ni hakkina a duk sanda na nema, hakan ne zai tseratar da ke daga siraɗin tsinuwar mala'iku". Ya janyo hannuna yana cewa"Daure kin ji, nan gaba kaɗan za ki saba, gobe ma kin ga iya na dare ne, sai kuma na gabannin asuba, tun da da rana muna azumi". Kamar zan yi kuka, haka na miƙa kai zuciyata cike da fargaba, da gaske na gaji, kuma wallahi na fara hasashen zan ma iya buɗewa na zama kamar ƙofar gari matuƙar na cigaba da zama da wannan mutumin. Muna cikin cin abinci yake cewa"Assayyada sai fa kin dage, domin zama da mai irin larurata da fari akan ɗan sha wuya, amma yana da daɗi idan ka saba, kin ga dai ita waccen matar cewa ta yi ba za ta iya ba, duk yadda nake sonta ƙarshe haka ta fita fit daga raina wallahi, to duk macen da ba za ta taimake ka ba ina ranar zama da ita?" Na ce"Kenan ni ma nan gaba idan na gajiya zan fita daga ranka?" Ya yi murmushi ya ce"Ban ce ba, amma dai ki sani ba ni agajin gaggawa a duk sanda na nema shi ne tikitinki na shiga zuciyata". A raina na ce'Ashe kuwa har mu rabu bazan ko leƙa zuciyar taka ba, domin ba a taɓa cigaba da tafiya a haka ba'. Ya ce"Ni fa saboda ban ɓoyewa ogana na kasuwa larurata ba, shi yasa ya ba ni damar zuwa da rana gida na dinga sauke nauyi, hala muka yi da waccen matar, amma ƙarshe da ta fara taɓarɓarewa ko na dawo sai ki ga ta bar ni a wahale, haka zan ja jiki na koma, daren ma wataran ta kulle ƙufa sai dai na kwana a falo, ƙarshe ma sai ta fara yin ƙunzugun ƙarya". Ya girgiza kai ya ce"Ya subhanallah! Wato Maraƙisiyya ta gana min azaba, don Allah Assayyada kar ki zama kamar ita, ki daure ki cika dokokin aure da sharuɗansa". Na ce"Allah Ya ba ni iko". Ya ƙaraci iyayinsa da surutu ya fita, yana fita aka kawo wuta na saka wayata a caji, na kunna data, abun mamaki sai ga saƙon Sadam, sai da gabana ya faɗi, na duba na ga sallama ya yi min, ban amsa ba, kuma yana online, har zan kashe datar na ga ya fara typing, ya rubuto"Sayyada amaryar ustazai, ashe kin yi aure, ba ni da labari sai jiya, to Allah Ya ba ku zaman lafiya ya kawo zuri'a ɗayyiba". Tsaki kawai na yi na danne lambar tasa na goge ta daga whatsApp ɗin, na fita ina wanke-wanke ina tunanin rayuwa, ni ban ga amfanin Sadam ya yi min fatan alkhairi ba, tun da na yi aure babu sauran wata alaƙata da shi, don haka na yanke idan ya sake yi min magana zan taka masa birki. Sai da yamma 'yan'uwana suka zo, su huɗu ne har da Anisa, taliya na dafa musu kamar yadda ya ce, suka kawo min kayan gara, buhun shinkafa babba, katan ɗin taliya da na macaroni, katan ɗin indomi, sai galan ɗin man gyaɗa, magi, spices ɗin girki da na shayi, har da su kuka da busasshiyar kuɓewa, daddawa, kanwa da dai sauransu, ga kuma cincin da dubulan fal bokitai guda biyu, sosai na ji daɗin kayan, bayan sun tafi na kira Baba na dinga yi masa godiya, ita ma Mama na kira ta. Kafin Ustaz ya dawo kamar yadda Sadam ya yi masa suna, na zauna na yi wa kaina karatun tanutsu, ko ba ni da dogon nazari dole na gane mijina matsolo ne, mammaƙonsa ya yi yawa, don haka dole na san dabarun da zan samo don ganin ulser ba ta kama ni ba, ko cuwa-cuwa dole zan fara don na dinga ƙoshi, a ganina tun da ba dafawa zan yi ya yi yawan da za a zubar ba, kuma ba wai zan dinga rabawa ba ne ai Allah ba zai kama ni da wannan ba, don haka na sungumi kwalin indomi na sauke kayana dake cikin sif na saka shi daga ƙasa, na mayar da kayan, da niyyar sai na dinga dafawa bayan ya fita, tun da ba ƙoshi za mu dinga yi ba, tunawa da na dafa guda ɗaya ɗazu ba bisa ƙa'ida ba ya da ni farke kwalin na ɗakko ɗaya na mayar kitchen ɗin. Da ya dawo ya ga kayan ya dinga jera Alhamdulillah, ma sha Allah, sai ga mutum ya ɓarke da surutu, yana tsara yadda za a dinga sarrafa kayan abincin nan, ya dinga janyo addu'o'i wa iyayena ina amsawa, kuma addu'ar ta yi min daɗi. Da ya fita sallar isha'i kafin ya dawo na juye sauran taliyar da ba su cinye ba, na cinye, da ya dawo muka ci sauran shinkafar rana, ya ce na ɗakko Qu'ani, na ɗakko ya tambaye ni inda na tsaya, na faɗa masa na yi sauka, amma ta biye ce, ya ce to za mu fara hadda, kullum zai dinga ɗora min aya biyar, muka fara daga Suratul baƙara, ba mu tashi ba sai da na haddace, sannan ya shiga wanka, yana fitowa ni ma na shiga, kafin na fito ya yi shirin bacci, wallahi har fargabar kwanciya a gadon nake yi, haka dai na kwanta ina saddaƙarwa, ya ce "Assayyada akwai azumin gobe Litinin sai ki ɗaura niyya". Na yi shiru saboda tsakani da Allah ni dai ba na yi, kuma ban yi niyya ba. Ya ce"Dama akwai indomin nan ɗaya da rabi ko? Sai mu yi sahur da ita, kin san akwai albarka a cikin sahur". Na ce"Amma ni fa ba na yin azumin Litinin da Alhamis" Ya ce"Me yasa?" Na ce"Kawai, ai niyya ne, ba dole ba ne". Ya ce"Amma ai sunna ne Assayyada". Nan ya tisa ni a gaba da wa'azi tare da kwaɗaitarwa a kan ladan dake cikinsa, har sai da na amince zan dinga yi, sannan ya janyoni ya shiga sana'arsa, tun ina daurewa har na fara roƙonsa, yana ba ni haƙuri da cewar gobe babu na safe babu na rana don haka yana da fa'ida yanzu a yi nisan zango, wallahi ustaz dai sai da ya ga na fara jan numfashi kamar zan fita a hayyacina sannan ya ƙyale ni, ya shiga jero min godiya yana cewa"Da a ce za a hasko miki ɗumbin ladan da muka samu a yanzu da kin ce a koma fagen fama, na faɗa miki tamkar fa an jere arna guda saba'in ne, yanzu a nan anya kuwa mun kashe guda goma? Idan a zahiri ne aka ba ki bindiga ai sai inda ƙarfinki ya ƙare, to da haka za ki dinga hasashowa sai kin fi ba ni haɗin kai". Ina kuka na ce"Idan ba ka kashe arna ba ai za ka kashe mumina, a gaskiya idan aka cigaba da tafiya a haka zan cutu". Ya ce"Yi haƙuri daure Assayyada ba za ki cutu ba da yardar Allah". Da ƙyar na dafa ruwan zafi na shiga ciki, na ɗan samu sauƙi, na kwanta, da ya tashe ni sallar dare na ƙi tashi, na ce kaina ciwo yake yi, ya zo ya yi min kamun kai, yana ta yi min sannu, ƙalau nake kawai bacci ne a idona, ga jikina duk tsami, sai shi ya dafa indomin ina ji yana ci bai tashe ni ba, sai da lokacin sallah ya yi ya tashe ni, ya ce na tashi yanzu za a kira sallah, azumin kuma na haƙura tun da ba ni da lafiya, ya tafi masallaci. Wani abun murna da farinciki ina zuwa banɗaki don yin fitsari na ga period ɗina ya zo, farin ciki ya mamaye ni, ko banza zan huta na kwanaki uku, sai na ga yadda zai yi da jarabarsa ai. Yana dawowa daga masallaci na faɗa masa zuwan baƙon nawa, ya ce"Subhanallah!". Ya ce"Dama idan ana azumi irin wannan sai dai a raba ɗaki, ni bari na je daga falo". Ya tafi falo ni kuwa na koma baccina. Sai da gari ya yi haske, ya fita ya siyo min biredi da suga na Naira ɗari, sai madara guda ɗaya babu milo, kafin ya fita na ce masa ina son shiga maƙota a gaisa, ya ce"Amma tun yanzu? Kin ga fa ban fiya son wannan shige-shigen ba, ba shi da wata fa'ida, na dai fi gane idan kin ji wani abu ya fara, haihuwa, biki, rashin lafiya sai ki shiga". Na ce"To". Ya ce"Amma dai ki shiga ɗin, kar ki daɗe". Na ce"Me za a dafa?" Ya ce"To kin ga ba don ba kya azumi ba ai da shinkafa gwangwani ɗaya da rabi ma ta ishe mu, amma yanzu dole lissafin ya canza". Ya yi jim kafin ya ce"Ba za ki iya cinye rabin taliya ba, To ina ga ki raba taliya gida uku sai ki dafa kashi ɗaya ki ci, da daddaren kuma sai ki dafa mana shinkafa gwangwani ɗaya da rabi ko?" Nan ce"To". Sai bayan ya fita na shiga kitchen ɗin, sai na ga indomi ɗaya ya dafa ya bar rabin, kuma ya cinye ta tass, na ɗakko tawa na dafa guda ɗaya, na tafasa shayin na sha da biredi sannan na ci indomin. Wajen ƙarfe goma na ɗauki ATM ɗina na fita, na fara shiga maƙota muka gaisa, yawanci duk manya ne, wacce na ga kamar sa'ata ce ita na tsaya muka yi fira , har nake yi mata ƙorafin rashin shigiwarsu, tun da su ya kamata su fara shigowa kafin ni, ta ce"Hmm, ai gidan naku ne ba koda yaushe ake shiga ba". Na ce"Ban gane ba". Ta ce"A'a, da na ga rufewa kike yi ne dai, shi yasa na ce haka". A yadda na lura da magana a bakinta, kawai dai ba ta don faɗa mini ne, na yi mata sallama na tafi, wajen me P.o.s na je na ƙwalulo kuɗin cikin account ɗina dubu bakwai, na sayi suga na dubu ɗaya, madarar gari gwangwani huɗu, na haɗu da me kifi na siya na dubu ɗaya, na koma gida na yi jollof ɗin rabin taliya da kifi, na ci na ƙoshi, na rage 'yar kaɗan, da yamma na ƙarasa abata, sannan na tashi na ɗora jollof ɗin shinkafa, gwangwani biyu da rabi na dafa a maimakon ɗaya da rabi da ya ce, kuma sai ga shi mun cinye ta tass. Aka zo bacci, na yi zaton zai juya min baya ne ya bar ni yau na yi baccina cikin salama kamar kowace mace da take auren lafiyayye, sai ya ustaz ya ce ba haka ba, abubuwan da ya dinga yi min a ƙoƙarinsa na samawa kansa nutsuwa sai da na ji dama ba na fashin sallah na ba shi duka kawai na huta. Da safe ma haka ya tisa ni da romance, da rana dai yau bai dawo ba. A haka rayuwar tamu ta fara miƙawa, a hankali ya koya min yawan karatun Qur'ani, tun da kullum sai ya ba ni hadda na kawo masa ita, sannan sallar dare har na saba, idan na ƙi tashi ya shiga shafa min ruwa a fuska yana kwaɗaitar da ni ladan dake cikin tsayuwar dare, abinci kuwa yadda ya tsara min ba haka nake yi ba, dafawa nake wanda na san zai ishe mu, mahaifiyarsa ta zo gidan sau ɗaya, ƙannensa mata sun zo su ma, abu ɗaya ne ya fara haɗa mu faɗa shi ne yadda na gajiya da yawan buƙatarsa, idan ya matsa min da wa'azi sai na saka masa kuka, kuma na ƙi zuwa ɗin, wataran ya rabu da ni wataran kuma ya yi ko ba na so, sai dai ya dauki fushi da ni. [11/10, 5:34 pm] Sadiya Abdulrazak: LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, KU YI MIN ADALCI KU BIYA NI HAKKINA. 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 18 Duk maƙotan da na shiga babu wacce ta biyo ni, ko yara babu wanda yake shigo min, sai kace mugun abu, wataran sai na gaji da zaman kaɗaicin, idan na tambaye shi zan shiga sai ya hau yi mini wa'azin babu gaira babu dalili, har da na cewa "ka da ku yi fita, fita irin ta jahilan farko' ga shi idan ya tisa ni a gaba da wa'azi mai razanarwa a kan bijirewa umarmin miji duk sai na firgice, da wannan yake cuta ta, na bi umarninsa ko ba na so, ɓangaren abinci dai ba na biye masa, dafa wanda zai isa nake, yanzu sai na ci na ƙoshi ma kafin ya dawo, saboda na ga idan na zage na ƙoshi a gabansa wannan ma laifi ne, sai ya hau nasihar an ce a raba ciki gida uku. Ƙarshe dai da na gaji na fara shiga maƙota ba tare da sanin shi ba, wannan wacce take sa'ata gidanta nake shiga, sunanta maman Haneefa, sai mu sha firarmu, amma sam ba ta shigowa gidana ni, wataran da na ritsa ta da tambaya sai take ba ni labarin ai ita ƙawar tsohuwar matar Ustaz ce, sun yi zaman mutunci sosai da Maraƙisiyya duk da wata uku kawai ta yi a unguwar, tun tana ɓoye Ustaz hariji ne har aka gane, saboda a lokacin ba shi da lokacin dawowa daga kasuwa, safe, rana, dare koyaushe dawowa yake, ya tisa ta a gaba, sai da kowa ya lura ba ta iya haɗe ƙafafunta a buɗe take tafiya, kuma kana kallonta ka san tana cikin damuwa, har dai ta fito ta faɗa mata ga yadda mijinta yake. Na ce"To amma maman Haneefa don kin san halinsa mene ne na cewa ba za ki shiga gidansa ba". Maman Haneefa ta ce"Hmm, ai ba ki ji abubuwan da suka biyo baya ba ne". Ni kuwa har da gyara zama na ce"Mene ne ya faru?" Ta ce"Sayyada Maraƙisiyya ta so zama da malam Ashir sosai, abun ne kawai ya fi ƙarfinta, ina nuna mata ba za ta iya ba su rabu kawai, ita tana nuna min ita ce ta gaza, ta sa na samo mata maganin sanyi da na tadawa mace sha'awa, tana ta sha babu sauƙi, sai ta nemi a samo wanda zai rage masa sha'awa, na tambayi wacce take siyar mana da magani ta ce akwai, ta siya, to a ranar na kai mata ina yi mata bayanin yadda maganin yake, an ce idan ta dafa masa shayi da shi, abun zai zama kamar lagwani har sai bayan sati biyu, nake ba ta shawarar idan ta yi ta huta na sati biyu, sai ta ƙyale shi ya tashi idan ya ɗana na kwana biyu sai ta ƙara kwantar da shi, wallahi tsautsayi Sayyada, ashe ya dawo gidan yana ƙofar ɗaki yana jinmu, sai ji muka yi ya fara Subhanallah da Innalillahi, ni dai kamar na nitse a wajen, da ƙyar na iya fitowa daga ɗakin, ai kuwa ya ce idan ya sake gani na a gidansa sai ya faɗawa mijina zan kashe masa aure, kuma yanzu ma sai ya haɗa ni da Allah, daga ranar ban sake shiga gidan ba, ita ma ba ta sake shigowa ba, ashe mutumin nan ƙwace wayarta ya yi, kuma yake kulle ta a gida". Tsoro ya kama ni, don na hasko a ce ni ya yi wa haka, na ce"Kullewa kuma?" Ta ce"Wallahi, ranar dai da ta gaji ta kira ni ta katanga take faɗa min, ta ce takarta yake kamar zai kashe ta na taimake ta, shi ne na je na sami wani na biya shi, aka yanke mukullin, na shiga na same ta a jigace, ni da kaina na haɗa mata kayanta na ce ta tafi gida, tsakani da Allah aure irin wannan akwai cutuwa, kowace ƙwarya da abokin burminta, kamata ya yi ya samu daidai shi, muna cikin haɗa kayan ya zo gidan, ita kuwa ta ce wallahi sai ta tafi gidansu, ya riƙe ta, ta dinga zagin shi, ni kuma ina faɗa masa gaskiya, na ce wallahi idan bai rabu da ita ba, ta kai shi ƙara Human right a bi mata hakkinta, ke na dai zaƙarlale sosai fa, da ƙyar dai ya ƙyale ta ta tafi, na raka ta har gida, a gidan ma ai ta daɗe kafin ya haƙura ya sake ta, tun daga lokacin na yi alƙawarin duk wacce zai auro ba zan shiga gidansa ba, su kuma sauran mutane abin da ya sa kika ga suna hana yaransu shiga, a gaskiya akwai ranar da maman Ihsan ta aiki ɗanta gidan, kin san yaro ba hankali, ya je ya shiga har ɗaki, ya same su turmi da raɓarya da ranar Allah, ya faɗawa abokansa, yara duk wanda ya je gida sai ya ba da labarin an je gidan Amarya an ganta ba kaya ita da mijinta, shi ne kowace uwa ta zaunar da nata ɗan ta yi masa kyakkyawan gargaɗi, shi yasa har yanzu babu me shiga". Sayyada ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Ikon Allah, ki ce dai ke kika taimaki Maraƙisiyya". Ta ce"Uhm ai ni na yi mamaki ma da ya bar ki kike shigo min". Na yi murmushi na ce"To ai wanann ya wuce". Da son jin gulma ta ce"Kuma ke kina iya zama da shi ba ruwanki". Na ce"Ina iya ƙoƙarina". Muka taɓa fira na yi mata sallama na koma gida. Na zauna na yi shiru, bayan jin labarin nan yaƙe kawai na yi wa maman Haneefa, tsakani da Allah na ji kunya na ji takaici, wallahi ba na burin tonawa mijina asiri na faɗawa duniya ga larurar shi, ashe ni kowa na unguwar tsirara yake kallona an riga an sani, sosai na ji baƙincin wai an taɓa ganin shi da matarsa, na rasa ina zan kai kunya da takaici, da a ce na san da wannan labarin da ba zan shiga gidan kowa ba a maƙotan, tun daga lokacin kuma na yanke ba zan shiga gidan kowa ba, gara na yi rayuwata ni kaɗai, don haka na gyara zaman kaɗaici. Ina iya ƙoƙarina na ganin na jure jarabarsa, duk ina ina cutuwa, amma shi ba ya gani, a hankali na lura abun nashi gaba ma yake yi, yanzu bayan an yi kafin a kwanta, sai ya tashe ni tsakar dare an sake yi, sannan a yi sallah, wannan sallar ni dai na san wataran ba lada nake samu ba, saboda dole yake min, wataran na gaji bacci nake ji, ba a son raina nake yi ba, sannan da asuba ya a dawowa daga masallaci zai sake yi, to wataran bayan ya karya kafin ya tafi kasuwa sai ya sake kirana, sannan ya dawo da rana, da yamma ma idan ya dawo da wuri bai kai magriba ba sai ya yi ko kaɗan ne, Alhamis da Litinin ne kawai nake samun sassauci, lokaci ɗaya na firgice, duk na rame komai ya daina yi min daɗi, wataran sai na zauna na yi ta kuka, ga shi na kasa faɗawa kowa damuwata. Ana cikin wannan ƙadamin ne kuma na samu ciki, wannan ma ba mai laulayi ba ne kamar na gidan Sadam, don da rashin zuwan period ɗina kawai na gane na same shi, don a wannan rayuwar zuwan period ɗina ba ƙaramin abun farinciki ba ne, ko yaya ne wajen nan yana hutawa na 'yan kwanaki, to na ga wata ya zo ya wuce ban yi ba, don haka na siyo tsinken gwaji na gwada, ya nuna ina fa ciki, farinciki ya kama ni, saboda ina masifar son haihuwa, wallahi sai da na ji ƙaunar Ustaz kaɗan a cikin raina, saboda ta wajensa na samu abin da nake nema, wanda Saddam ya tauye ni ya so ya saka ni a layin marasa rabon haihuwa. To daga nan ne fa dabara ta faɗo min, na fara narkewa ina cewa ba ni da lafiya, sai yana nan sai na tsiri amai na ƙarya, ko na lulluɓa na dinga karkarwar ƙarya na ce zazzaɓi nake yi, har dai ya kai ni asibiti aka tabbatar da cikin jikina, da fari ya ba ni kulawa, ya yi haƙuri ya ajiye jarabarsa, sai dai idan ya kasa jurewa ya yi sau ɗaya da daddare, hakan ya sa na sake narkewa duk da ina ganin yadda duk ya rasa nutsuwarsa. Shigowar yanayin sanyi ne ya sake zabura shi, ya daina tausayin rashin lafiyar ƙaryar da nake yi, aka koma gidan jiya, tsoro ya kama ni, tsakani da Allah lallaɓa cikin jikina nake yi, don gani nake fyaɗen ƙarshe da Saddam ya yi min a ranar da ya sake ni shi ne silar zubewar cikina, don haka dole na kare wannan duk da Allah ne me karewa, duk yadda nake nuna masa ya ɗaga ƙafa saboda wannan cikin kar ta samu matsala ya kasa fahimtata. Yau ma bayan ya dawo daga masallaci ina bargo bacci tana gizgata ya shigo bargon, na yi saurin tashi na ce"Don Allah Malam ka tausaya min haka, gaskiya na gaji". Ya ce"Subhanallah! Wai da ladan kika gaji? Assayyada zai iya faruwa a ce a ranar lahira, an gama hisabi, ana auna ladanki da zumubinki a sikeli, a ce saura kaɗan ladanki ya rinjayi zunubin, ki shiga aljanna, ayyukanki na alkhairi duka sun ƙare, wannan rana ce da ko mahaifanki ba za su iya ba ki kyautar lada ko guda ɗaya ba, saboda kowa ta kansa yake yi, wato bi ma'ana nafsi-nafsi, kina cikin wannan halin kwatsam sai ki ji an ce, ga ladanki nan na taimakon mijinki da kika yi kuka raya sunna, don Allah ya za ki ji? To shi yasa shi aikin lada fa ba a raina shi". Hawaye kawai nake yi, zuciyata na zafi, na ce"Akwai hanyoyin samun lada da dama, in sha Allah zan shiga aljanna ko ba ta wannan fannin ba, kai malami ne, kana da sani, ka san aurena da kai akwai cutarwa a cikinsa, tun da dai halittarmu ba ɗaya ba, Allah Ya san da haka shiyasa da ya halicci maza masu irin halittarku, sai ya yo mata su ma masu irin halittar, don a samu daidaito da kuma adalci a tsakanin ma'aurata, don Allah don Annabi ka yi min adalci, ba na cikin mata masu yawan buƙatuwa, ina da rauni ta wannan fannin, ka taimaka ka yi min adalci". Na fashe da kuka. Ya yi shiru kamar jikinsa ya yi sanyi, ya ce"To yanzu kenan ya kike so a yi? Watanninmu uku da ke Assayyada, ya ci a ce kin saba, ba san ba haka kike ba, amma ai sabawa ake yi". Na ce"Tsakani da Allah idan shari'a ce aka kawo maka matsayinka na Malami wannan hukuncin za ka yanke?" Ya ce"To me kike so na yi bayan wannan?" Na runtse ido hawaye suka zubo ina auna maganar da zan faɗa, gabana yana faɗuwa na ce"Don Allah mu rabu kawai, tun da zaman aurenmu akwai cutuwa, ka sawaƙe mini". Nan take ya fara"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! La ila ha illallah! Subhanallah". Ya dinga girgiza kai kafin ya ce"Subhanallah! Kaiconki Ya Assayyada, yau kin aikata zunubi mai girma, wai ni kuwa kin yi islamiyya? Kin san hukuncin macen da ta nemi mijinta ya sake ta?" Na sunkuyar da kai na ce"Amma ai ni da dalili, ka fi ƙarfina, shari'a ba ta ce a yi irin wannan zaman ba". Nan ya shiga karanto min ƙauli da ba'adi, wa'azi na son zuciya, da hujjojin kare kai masu rauni, har jikina ya yi sanyi, na dinga kuka, ya ce"Assayyada kukan ya isa haka, yana da kyau ki nemi yafiyata, duk da dai ma idan ta ni ne na yafe miki, wallahi la ba'asa na yafe, to amma ya za ki yi da hakkin aure? Kin yi wa Allah laifi, ki nemi yafiyarsa, kuma dole sai ki nuna nadama shi ne kika tuba, bi ma'ana wato ainahin ki tabbatar da ainahin shi Annadamu ala ma fata, wato yin danasani a kan abin da ya wuce, to a nan sai ki yi tunani, ta ya za ki yi danasanin? A nan kuka ba shi da muhalli a lamarin danasaninki, ki miƙa wuya shi ne nadamarki, bi ma'ana ki yarda da ni mijinki kuma ki daina guduna a duk lokacin da na buƙace ki". Haka na miƙa wuya ba ni da yadda zan yi, da irin wannan yake kashe min jiki ya yi ta cutata. Wani lokacin sai na tsiri aiki na ƙi shigowa ɗakin, idan ya kira ni na ce aiki nake yi, nan ma da ya tisa ni a gaba da wa'azin da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce ko mace tana gasa gurasa ne mijinta ya neme ta ta katse ta ba shi hakkinsa, sai ya ɗora da faɗin idan kuma ban yarda ba ya yafe min sai na je na nemi yafiyar Allah don shi na yi wa laifi ba shi ba. Na sha rufe masa ƙorafa na ce sai dai ya kwana a falo, amma kamar tsohon maye sai ya zo window ya dinga karanto min wa'azi mai razanarwa, da zabar wuta nau'i-nau'i, a dole nake buɗewa na yarda da shi, sai dai na yi ta gursheƙen kuka. Da na ga abun yana neman wuce gona da iri, tun da gabana duk ya buɗe, na fara tusar gaba, abin da a baya ban taɓa yi ba, to yanzu na buɗe kuma tun da aka yi auren ban taɓa amfani da wani maganin matsi ba ko na ni'ima, ga shi kullum ƙafata a buɗe, don haka ban yi mamaki ba, kuma ba ni da niyyar neman maganin, saboda so nake ma ya ji rashin daɗi ko zai ɗaga min ƙafa, amma abu kamar ana ƙarawa zuma suga, sai na narke sosai na fara rashin lafiyar ƙarya, na kira Mama ina ta kuka na faɗa mata ba ni da lafiya sosai kamar zan mutu, sai ga ta a ranar ta zo gidan, da ta ga yadda na rame hankalinta ya tashi, dama duk sanda na je gida sai ta tambaye ni damuwata, sai na ce mata babu komai, duk don saboda kar ta ji halin da nake ciki ta faɗawa Baba, shi kuma ya yi zargin fitina ce kawai da rashin son zaman lafiya ya da na ce haka, to amma yanzu an kai magaryar tuƙewa, don haka na fashe da kuka ina faɗawa jikinta da faɗin"Mama don Allah ki tafi da ni, ba zan iya zaman auren nan ba mutuwa zan yi, zai kashe ni, rayuwata yake nema da ta ɗan cikina". Hankalinta ya kara tashi, ta ce"Ban gane ba, me yake yi miki? Ciki ne da ke dama?" Na nemi kunyata na rasa, na kwashe komai na faɗa mata, tuni ita ma ta fara kuka tana cewa"Sayyada ba ki da hankali za ki yi shiru ki zauna da miji irin wannan? Shikenan kin tashi daga aiki ya kashe ki, ya cuce ki". Na ƙara ruɗewa na tsananta kukana. Ta ce"Me yasa ba ki faɗawa kowa ba? Wannan fa cuta ce, bai halatta mai lafiya ta zauna da shi ba". Na ce"Mama Baba nake tsoro, ina so na yi masa biyayya, ba na so ya ce na ƙi karɓar zaɓinsa, ya riga ya yarda da shi, ya ce duk wata fitina da za ta taso sai dai daga ɓangarena". Mama ta dinga salati ta ce"Wannan wace irin ƙaddara ce?" Na ce"Mama taimaka ki tafi da ni gida don Allah, marata ciwo take yi, ba na so na rasa cikin nan, idan na haihu sai na dawo ya kashe ni, ko babu komai na samu mai yi min addu'a da kuma abin da za a gani a tuna da ni ko bayan raina, don Allah Mama ki tafi da ni". Mama ta yi shiru kamar mai tunani, kafin ta ce"Sayyada ina fargabar yadda Babanki zai ɗauki batun nan, ki bari na fara tattaunawa da shi tukunna". Ai kuwa na riƙe ta gam, na dinga rusa mata kuka, har ta yarda ta taya ni haɗa kaya muka tafi gida tare, a raina kuwa ayyanawa nake na bar gidan nan har abada. [12/10, 3:53 pm] Sadiya Abdulrazak: LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, KU YI MIN ADALCI KU BIYA NI HAKKINA. 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 19 A daidaisahu ma sai kuka nake tana rarrashina, sanda muka ƙarasa gidan Baba ba ya nan, don haka nake ta fargabar dawowar tashi, can da na daidaici Ustazuna ya kusa dawowa cin abincin rana, sai na yi masa massage na ce masa ina gidanmu kuma na taho da mukullin, babu jimawa kuwa ya kira ni, na ɗauka, ya ce"Assalamu alaikum, Assayyada lafiya? Wane babban lamari ne ya faru da har kika fita ba tare da izinina ba?" Na ce"Na gaji ne, ba ni da lafiya kuma na ga hakan bai dame ka ba, buƙatarka kawai ka sani, don haka ba zan iya ba, na gaji da aurenka". Nan take ya fara jero"Subhanallah! Subhanallah, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!". Na kashe wayar, ya sake kira na ƙi ɗauka, ya yi min kira ya fi goma, ƙarshe ma na kashe wayata, ai ya san hanyar gidan namu ya zo ya karɓi mukullin ƙaddararren gidansa. Bai zo ba da rana, sai can wajen magriba ya zo, ya aiko ana sallama da ni, don har lokacin ban kunna wayata ba, Mama ta leƙo ɗakin da nake a zaune ina nazari ta ce"Ina ga shi ne ya zo, ki leƙa ki ba shi mukullinsa". Na ce"Mama don Allah ki kai masa, walla tsoro nake ji, gani nake kamar zai riƙe ni". Ta ce"Ni za ki aika kai masa mukullin kenan? Kuma riƙe ki sai idan ke kika so". Ta koma harkar gabanta, na tashi ina jin kamar zan rusa ihu, na saka hijjabi na ɗauki mukullin na fita, a zaure na same shi yana ta shafa gemu, yana gani na ya taho ya ce"Assayyada lafiya? Me ya yi zafi haka?" Na ce"Babu komai, ka karɓi mukullinka". Ya ce"Subhanallah, shin kin manta da cewar duk matar da ta fita ba tare da izinin mijinta ba Mala'iku suna tsine mata a duk wani taku ɗaya da za ta yi". Takaici ya kama ni na ce"Ai a adaidaitasahun na zo ba takawa na yi da ƙafata ba". Zai yi magana na katse shi da faɗin"Don Allah ka tafi, ni dai na gama aurenka haka". Ya riƙo hijjabina yana cewa"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Ki dubi Allah Assayyada ki yi haƙuri, idan kika guje ni ya kike so na yi? Na ji zan sassauta kaɗan, zan rage in sha Allah". Na fizge hijjabina na shiga gida, yana ta kirana muryar nan a make kamar an matse shi, ban ko juyo ba na shige gida. Ustaz ya ƙi barin unguwar nan, bayan ya yi sallar magriba zama ya yi a ƙofar gida ya jira dawowar Baba, bayan sun gaisa Baba ya ce"Ya Sayyadar? Kuna zaune ƙalau ko?" Ustaz ya sunkuyar da kai cikin jin kunya ya ce"Ai tana ciki, mun ɗan samu saɓani ne, shi ne ta taho gida ta ce ba za ta koma ba, duk da dai lamarin ba laifina ba ne amma na yafe mata Baba, a dai ba ta haƙuri ta zo mu tafi". Abun ya bawa Baba mamaki, shi duk ya yi zaton Sayyada ta haƙura tana zaune da mijinta ƙalau, ashe ta ce bai isa ta bi umarninsa ba, nan take ransa ya ɓaci, ya ce"Malam Ashir tun yaushe kuke samun saɓani ba ka faɗa min ba?" Ya sake sunne kai ya ce"Alal haƙiƙa Baba ba mu taɓa samun saɓani ba sai yanzu, shi ma kuma na san za mu sasanta ma, e ba sai kun shiga ba, bi ma'ana dai inda za a ba ni ita ta koma da komai zai wuce". Baba ya ce"To mene ne ya haɗa ku?" Ya ce"A'a fa Baba na yafe mata ni har zuciyata, tada zancen ma ba shi da daɗi". Baba ya ce"Ina zuwa". Ya shiga gidan ransa a ɓace yana ƙwala kiran Sayyada. Ganina kwance a jikin Mama tana ba ni kunu a baki ina sha ya sa shi dakatawa, ya ce"Ke Sayyada me ya kawo ki gidan nan? Mene ne haka?" Mama ta ce"Da farko ka fara kallonta ka gani". Ta ɗaga ni tana jijjiga ni, dayake akwai hasken wutar nefa tarr yake kallona, ta ce"Ka kalle ta da kyau a haka muka aurar da ita, ka kalli ramar da yarinyar nan ta yi, ka kalle ta sam ba ta da nutsuwa, ta firgice, wannan auren ban ga ranar shi ba, wannan ba miji ba ne, gaskiya a raba auren nan kawai". Baba ya ce"Tambaya nake yi fa mene ne ya haɗa su? Me kika yi masa?" Na ce"Baba ba komai, ba faɗa muka yi ba, ba ni da lafiya ne sosai shiyasa na taho gidan". Ya ce"Yau ga shirmen banza saboda ba ki da lafiya sai ki taho gida? Kanki farau?" Na ce"Baba jiri nake ina faɗuwa fa, kuma a haka zai saka ni girki da aikin gida dole". Mama ta karɓi da faɗin"Shekarar yarinyar nan nawa da aure Allah bai ba ta haihuwa ba? Sai yanzu ta samu kuma sai a barta cikin bauta har cikin ya zube?" Baba ya ce"Ke ɗin wace irin wahala ce ba kya sha idan kina laulayi? Lalacin banza, wannan ya kai abin da zai sa ta kama hanya ta dawo gida babu izinin mijinta? To maza tashi ki bi shi". Mama ta ce"Ba fa wannan ne maƙasudin zuwa gidan ba, kuma don mace tana shan wuyar laulayi babu kulawar miji ai ba za a ce a raba aure ba, ka samu mutum sama ta ka babu binciken me ya raba shi da tsohuwar matarsa ka wanke taka 'yar ka ba shi, to ga shi nan ai yana neman rayuwarta". Baba ya bi ta da kallon neman ƙarin bayani, shi ma ƙarfin hali kawai yake yi, amma ramar Sayyada ta ba shi tsoro, ya zauna ya ce"Ban gane yana neman rayuwarta ba, na fa lura ke za ki ɗaurewa yarinyar nan ki hana ta zaman aure, wai idan an ce ta sake zama bazawara a karo na biyu mene ne ribarki ne?" Mama ta ce"Mijinta hariji ne, ta yi iya ƙoƙarinta na ganin ta daure ta gaji, nawa Sayyada take? Ta yi ƙanƙanta da wannan juriyar ba za ta iya ba, cutarta yake yi". Kunya ta kama ni, na sunkuyar da kai ina hawaye, tare da fargabar hukuncin da Baba zai yanke a kan lamarina. Mama ta ɗora da faɗin"Ka san wane ne hariji, kai da kanka ka shige gaba ka kashe auren ƙanwarka Salamatu, kuma matsalar iri ɗaya ce da ta Sayyada, shin ƙullatar 'yarka da ka yi zai sa ka kasa ƙwatar mata 'yancinta? Wallahi ba za ta koma ba". Ta ƙarasa kamar za ta yi kuka. Baba ya zuba min ido kamar ba shi da abin cewa, kafin ya ce"Sayyada". "Na'am" Na amsa da muryar kuka. Ya ce"Ta nan kuma kika ɓullo? Kin rantse ba za ki yi zaman aure ba ko? To idan ma gidan tsohon mijinki kike hange ko aurenki ya mutu matuƙar ina raye kin gama aure da wannan yaron har abada, sai dai ko idan da rabo a tsakani rabon ya kashe ni sannan ku yi auren". Na ce"Wallahi Baba babu tunanin komai a raina, da zuciya ɗaya na karɓi auren nan, amma ba zan iya jurewa ba". Ya ce"Zan yi magana da shi, ni na san ba zai yi ƙarya ba, indai ya ce hakane kuma ya nuna halittarsa ce haka zan goyi bayan zamanki a gida kafin a san yadda za a yi, saɓanin haka kuma za ki bi shi ku tafi, kuma idan kika sake tada wata fitina a zamanku ba zan yafe miki ba". Daga haka ya fita daga ɗakin, na fashe da kuka Mama tana rarrashina. Ya koma ya samu Malam Ashiru kansa a sukunye, gabansa faɗuwa kawai yake, idan aka ce ya rabu da Sayyada tabbas zai shiga tashin hankali, sai yaushe kuma zai samu wata matar? A sanyin nan da idan ya busa yake jin kamar ana daɗa zabura shi zai sha wuyar zaman gwauranci, Baba ya ce"Malam mene ne matsalar ne?" Ya ce"A...ni dai a sanina babu wata matsala". Baba ya ce"Ta ce kana da larurar da ba za ta iya zama da kai ba, hakane?" Ya ce"Subhanallah! Wallahi Baba ba larura ba ce, itan ce dai nake tunanin tana da rauni, kuma hakan yana da nasaba da tata larurar". Ya muskuta ya ce"Baba ni lafiyayye ne, ita kuma na kula tana da ciwon sanyi, kuma mun yi magana na fahimce ta, sai na ɗaga mata ƙafa ma, har na ce mata zan siya mata magani, yanzu ma na siya to ganin ta samu ciki ne ya sa na ce tun da maganin yana da ƙarfi ta dakata sai ta haihu, tsakani da Allah Baba a ce gabaɗaya a jingine raya sunnar saboda wannan?" Baba ya ce"Ikon Allah, au wato yarinyar nan da gaske take ba za ta bi umarnina ba kenan". Ya ce"A'a Baba a yi haƙuri, ba haka abun yake ba, wallahi Sayyada tana yi min biyayya kuma muna zaune lafiya sosai, ina sonta tana sona, matsalarta ɗaya ce, kawai ta wannan fannin ne, take ɗan tauye min hakkina, shi ɗin dai za ta gyara sai a samu sasanci in sha Allah". Baba ya shiga gidan, Ustaz ya fara furta"Astagfirullah". Yana shiga ya rufe Mama da faɗa yana cewa"To ai kin ga irinta, yarinya ta zo ta shirya miki ƙarya kin hau kai kin zauna babu bincike, ashe ita ce ma take gudunsa a shimfida tana wahalar da shi, mene ne auren don ubanki?" Ya karasa maganar yana daka min tsawa, na saki sabon kukan tausayin kaina. Mama ta ce"Ai dole ta guje shi tun da ya fi ƙarfinta, kowa fa ya san wane ne hariji, ka tausayawa yarinyar nan, kar ta mutu garin ganin cewa sai ta yi zaman aure". Ya kalle ni ya ce"Ke Sayyada ba na son ƙara jin magana irin wannan mara tushe ballantana makama, ya faɗa min gudunsa ma take , saboda ciwon sanyi da ya yi mata katutu, kuma ya nema mata magani, me zai yi wanda ya wuce wannan? Allah Ya rufa miki asiri kin samu miji yaro mai hankali shi ne za ki saka tunanin ɗan iskan tsohon mijinki a ranki ko?" Kukana ya tsaya cak lokacin da Baba yake cewa"Maza ki tashi ki bi mijinki, ki koma ɗakinki! Idan kika sake zuwa gidan nan da sunan yaji ko shirmen banza za ki ga yadda za mu kwashe". Jikina ya ɗauki rawa, har bakina karkarwa yake yi, na kasa cewa komai sai kukan da nake yi kamar raina zai fita, ina ji Mama tana ta yi masa bayani ranta a ɓace, shi ma ya hau har sun fara fusata da mayar da martani mai zafi, na tashi na ja akwatin kayana ina ta kuka na fita daga ɗakin, Mama ta ce"Dawo Sayyada, babu inda za ki je, duk matakin zai ɗauka sai dai ya ɗauka, me yasa maza duka halinsu ɗaya ne, ba kwa yi mana adalci". Ko juyowa ban yi ba, sai da na kai zauren da yake a zaune a kan itace, na tsaya ina tsananta kukana. Ya taso yana "Subhanallah! Assayyada, me ya yi zafi haka, don Allah ki bari, ki yi haƙuri aure ibada ne, kuma dama raya sunna sai an daure, mene ne auren idan ba shi ba? Yi haƙuri mu je zan gyara kin ji?" Ya fita, na bi bayansa, ya tada babu dinsa na hau muka tafi, na tsaya da kukan, amma jikina bai daina rawa ba, kamar zazzaɓi zai kama ni ma, zuciyata kuwa kamar gasata ake yi da wuta, ji nake dama na faɗo daga babu ɗin nan na mutu na huta, ba don dai cikin jikina ba, wanda na ƙwallafa ran na haife shi. Yana ta tasbihi har muka ƙarasa gida, bayan mun shiga ya ya zauna yana ta ba ni haƙuri da faɗin"Assayyada na san na ɗan fi ƙarfinki, amma ke ma fa da naki laifin, bi ma'ana kin kasa buɗe zuciyarki ki karɓe ni ki yarda cewa ke ma za ki iya zama yadda nake, inda kin yi niyya da tuni kin zama irina, kin ga da an wuce wajen, yanzu tun da ciki ne da ke, kuma tun da har kika iya zuwa gida da wannan lamari mai girma na san kin kai ƙarshe ne, ki zaɓa a cikin sau ukun da muke yi ko huɗu wanne kike ganin za a soke? Ni kuna zan yi iya ƙoƙarina na ga daure an yi minus one, amma ban da na dare, domin shi ne lokacin da na fi samun nutsuwa". Na ce"Babu wani lokaci da za a rage, ka ƙara ma, ka dawwama kana taka ta don Allah, idan na mutu ai dai ba za ka taki gawata ba ko?" Ya ce"Subhanallah! Wato ainafin Assayyada har yanzu ba ki gama sanin darajar miji da aure ba, inda kina da sani da ba ki yi wa mijinki wannan gatsali ba, amma dai la ba'asa na yafe miki, kuma ni fa duk wannan abun ina yi ne don na ga na ba ki cikakken hakkinki ban bar wani gurbin da za ki ji kewa ba, amma tun da hakane la ba'asa, idan don ta ni ne ni fa zan iya haƙura ma na zuge tazugena, to kawai ina tuna cewa sunna ne, kuma shi ne auren, sannan jihadi ne, na sha faɗa miki tamkar ana yaƙi ne, ana kashe arna guda saba'in, shin ba kya kwaɗayin ladan da za ki samu ne?" Ban ce komai ba, har ya ƙaraci surutunsa, ya ce"Yunwa nake ji, me za ki dafa mana yanzu?" Nan ma dai ban kula shi ba, ya ce"Subhanallah! Wato Assayyada da a ce kin san girman hukuncin matar da ba ta bin umarnin mijinta da tuni kin doƙa kin fara roƙona gafara, duk da dai ko ma ba ki roƙa ba ni na yafe miki ma". Na ce"Ballantana ma ba zan roƙa ba, kar ka yafe ɗin, idan ka ga dama kar ka ɗaga min kafar na shiga aljanna, kai ba malami ba ne, mai son zuciya ne, mai ci da addini, Allah yana kallo yana sane, in sha Allah zan ta kai ƙararka wajen shi, shi ne zai bi mini hakkina". Na fice daga falon, na yi alwala na shiga ɗakin gado na yi sallah na canza kaya na kwanta. Ina jin shi a kitchen, sannan ya zo ya kawo min abinci ya ce na tashi na ci, ban san ma me ya dafa ba, don ko kallonsa ban yi ba, haka ya gaji da yi min nasiha ya fita da abincinsa, ina ga dai ta sha jinin jikinsa domin kuwa haka muka kwana ƙalau bai neme ni ba, da asuba ma bai kula ni ba, da safe sai na lura kamar ma wani kaffa-kaffa yake yi da ni, fuskarsa babu yabo babu fallasa, ba wai fushi yake yi da ni ba, na yi kwance na ƙi yin abin karyawa, sai shi ya dama koko, ya fita ya siyo waina, ya ci ya rage min, bayan ya fita na dafa farar taliya na ƙara na ci, to me waina guda uku za ta yi min da koko rabin kofi? Da rana ma na dafa shinkafa gwangwani uku, na ci na ƙoshi na saka sauran a kula na tura ƙarƙashin gado, na kwanta na ɓata rai, da ya dawo cin abinci na yi banza da shi, ya shiga kitchen ɗin ya dafa taliya, ya zuba min na ƙi ci, ya koma kasuwa, da daddare ya tafi sallar isha'i na ci sauran shinkafata, sai ga shi ya shigo da gurasa, ita ma na ƙi ci, duk hankalinsa ya tashi yana ta ba ni haƙuri wai kar yunwa ta lahanta ɗan cikina, na yi banza da shi. Kwana uku muna a haka da shi, shi duk a zatonsa ba na cin abinci, rana ta huɗu da daddare sai ga shi ya siyo tsire ya juye a faranti ya kawo min har da lemo, wannan ne na ɓata rai na ci, saboda ina marmarinsa, to abin da ba samu kake ba. Bayan mun kwanta sai mutum ya matso, na matsa, ya sake matsowa ya ce"Haba ya ke Assayyada, tun da kika ci tsire ai na yi zaton komai ya wuce kuma shikenan, ashe da saura?" Na yi shiru gabana yana faɗuwa, ya ce"Wallahi kwanakin nan da na ɗaga miki ƙafa ni kaɗai na san halin da nake ciki, yau dai na kai maƙura, a gaskiya ya zama dole ki ba ni hakkina ko ba kya so, indai kuma ba so kike na kauce hanya ba, bi ma'ana ta yi istimna'i, ke kuma ki kwana cikin tsinuwar mala'iku har sai kin wayi gari, ni wallahi na yafe miki ma, amma tsinuwar kawai nake guje miki". Ya ƙaraci wa'azinsa ban kula shi ba, da ya da gaske ba zan ce na amince ba, ban kuma hana ba, sai ya birkito ni, ya fara cim ma ƙudurinsa, kamar ya manta da ciki a jikina, da na gaji ban ce masa na gaji ba kamar yadda na saba, kuka kawai nake yi mai cike da ƙunar zuciya na tsantsar baƙinciki da nadamar yarda da aurensa, a raina ina tunanin shi ne bai yi min adalci ba ko mahaifina? [13/10, 7:20 pm] Sadiya Abdulrazak: LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, KU YI MIN ADALCI KU BIYA NI HAKKINA. 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 20 Da asuba ma bayan ya dawo daga masallaci haka ya min yadda ya so, ban kula shi, sai da ya yi iya yinsa, ban gaishe shi ba kamar yadda na saba, sai shi ya gaishe ni ban amsa ba, ya ce"Assayyada za ki dafa mana shayin ne ko na ɗora?" Na yi banza da shi, ya shafawa kansa lafiya ya dafa, ya sha ya rage min da guntun biredi, da zai fita ya ba ni ɗari biyu da hamsin, ya ce"Kasancewar yau ba zan dawo da rana ba, kuma na ga babu kayan miya, shi yasa na ba ki wannan, anjima sai ki saka babban hijjabi ki suturta jikinki ki fita nan gabanmu akwai mai siyar da kayan miya, sai ki siya, bi ma'ana attaruhu da tattasai na ɗari biyu, ita albasal wato albasa ta naira hamsin, kin san sunanta kenan da larabci, shi kuma attaruhu da tattasai larabawa suna ce masa fil-fil, ma sha Allah". Ko kallon shi ban yi ba, ya ɗora da faɗin"A bisa adalci da alƙawarin da na yi miki na duba na ga akwai buƙatar na daure na yi jarumtar rage round ɗaya a zamantakewarmu, shiyasa na cire wannan lokaci na rana, don haka ba zan dawo cin abincin rana ba, dama alal haƙiƙa a zahiri ba wai abincin nake buƙata ba, kawai don dai a raya sunnar ne, amma abinci ni kin san bai dame ni ba, ko kunu na siya na naira hamsin na zuƙe shi a leda cikin yana ɗagowa". Ya ƙaraci surutunsa ya fita daga gidan. Na kifa kai a kujerar da nake ina sakin kuka, Allah ne kawai ya san halin da nake ciki, sai kuwa matar da ta auri irin mijina, na yi kuka a ranar sosai, kukan baƙincikin halin Babana da ba zai tsaya ya fahimce ni ba, kuma a ranar na yanke cewar na gama kuka a auren Ustaz, na daina kai wa kowa ƙara zan zauna har sai na mutu, a ranar na kashe wayata na jefa a sif, ban siyo kayan miyan ba, shayin da ya bar min ma ban sha ba, na kwanta kawai ina tunanin yadda rayuwata take wakana, na san na yi laifi a baya, amma ai na yi nadama na tuba, ni na san auren Ustaz ƙaddarata ne da jarabawa, amma a yanzu na fara tunanin anya kuwa ba kamun Allah ba ne? Anya ba abin da na shuka nake girba ba? Zamanmu da Sadam nake tunawa, tabbas ya yi min cuta kala-kala, amma da ya tuba ya so mu gyara zaman me yasa ban yarda ba? Yanzu da wannan halin da nake ciki a wannan gidan me kama da kurkuku ai gara ma zama da kishiyar, tun da ban ga me matar Sadam ta tsare min ba, rabin abin da ya sa na ji zafin auren shi ne saboda tunanin za ta riga ni haihuwa, to ashe Allah Ya tsara ni ɗin ce dai zan riga ta samun ciki da Sadam, amma a garin shirmena cikin ya zube, wallahi a yau na ji inda za a mayar da bara bana da na yi haƙuri na zauna da Sadam, sai yanzu na gane ƙarya ma nake yi, Sadam ba fyaɗe yake yi min ba, wannan rayuwar da nake ciki yanzu shi ne fyaɗe na ainihi, tun da aka yi auren nan a ranar farko, kasancewarmu da shi ta farko ne kawai na san na ji shaukin abun, amma tun daga ranar ban sake fahimtar komai ba sai azaba kawai, na tsani sex gabaɗaya, gani nake ma ya riga ya kashe min sha'awata, ji nake kawai ba zan sake son kasancewa da namiji ba ko ba shi ba, na tsani namiji. Ban ci komai ba duk yunwar da nake ji, har dare, na yi azumin da babu lada, ana idar da sallar magriba ya dawo gidan, ya ƙaraso falo da nake a kwance, ya zauna ya fara shafa ni yana cewa"Assayyada na yi kewarki fa yau, na yankewa kaina hukunci mai tsanani, minus one ɗin nan anya zan jure kuwa?" Ban kalle shi ba, ban kuma hana shi ba, ya ce"Wai ni kam Assayyada me kike nufi ne? Na ga kin daina yi min magana gabaɗaya kin jingine ni a gefe, me na yi miki? Gaskiya ba na son wannan fushin, mu fa ma'aurata ne, idan akwai wani da kike zargin na yi miki ko ina yi miki buɗe baki za ki yi ki faɗa min ai, ni ba zan gane ba sai kin faɗa". Ya dakata da shafa ni ya tashi ya shiga kitchen, ya fito ransa a haɗe ya ce"Wai Sayyada me kike nufi ne? Kenan yanzu kin daina girki a gidan nan ko me?" Sai yanzu idonsa ya kai kan shayi da biredi da ya rage min, yana nan a inda yake, don yau ban yi ko shara ba, ba wanke-wanke, babu wanka, sallah kawai nake tashi na yi. Cikin tsawar da ban taɓa ji ya yi ba ya ce"Ke Sayyada! Ba da ke ake magana ba? Me yasa ba ki yi girki ba?" Ni ma a tsawace na ce"Ban yi ba ɗin kuma ba zan yi ba! Ba dai ina ba ka abin da ka aure ni domin shi ba?" Ya ƙure ni da wani irin kallo, na kau da kai ina ƙare haɗe fuska, ga yunwa tana sakaɗata amma don taurin kai ba na jin zan yi girki, ya yi ƙwafa ya fice daga gidan, sai bayan sallar isha'i ya dawo da ledarsa, bai kula ni ba ya zauna yana cin gurasar da ya shigo da ita, ya gama ci ya yi wanka ya shiga ɗakin gwado, wallahi na yi zaton zai yi fushi ya ƙi nema na, wajen ƙarfe tara sai ga shi ya leƙo falon, har yanzu fuskarsa a haɗe take, ya ce"Ke Sayyada, to tun da kin ce ba don ki dafa abinci na auro ki ba, la ba'asa na ji na yarda, sai ki taso a fara gabatar da abin da aka yi auren domin shi ko?" Ko kallon inda yake ban yi ba, ya koma, na yi zaton ma zuciya ya yi, sai ga mutum ya dawo ya shigo falon, zirr haihuwar uwarsa, gabana ya faɗi amma ban nuna ba, ya ƙaraso ya ɗauke ni cak ya kai can ɗakin gadon, ya yi yadda yake so, gani nake yau har da mugunta yake yi, baƙinciki kamar zuciyata za ta yi bindiga, ga yunwa da nake ji, ban san adadin lokacin da muka ɗauka a haka ba, ni dai ban so na dakatar da shi ba, na so ya kwana yana yi, ni ban san ma daɗin me yake ji ba a kiɗa da rawar da yake yi shi kaɗai, ban da ranar farko da nake ɗan jin shaukin abun da kuma son na kyautatawa mijina da na taya shi na ba da tawa gudunmawar don sama masa nutsuwa, wallahi duk sauran lokacin kwanciya nake kamar ruwa, amma na ga hakan ba ya damunsa ma, tun da dai bai taɓa ƙorafi ba. Ganin numfashina yana neman ɗaukewa kamar zan mutu ya sa ni fashewa da kuka ina ture shi, bai yi musu ba ya rabu da ni yana jero hamdala, sai da ya fito daga wanka sannan na tashi na fita daga ɗakin, jiri na ji yana kwasata kamar zan faɗi, ƙafafuna suka fara rawa kamar an kunna wata na'ura, tun da can ba ni da juriyar yunwa, don haka na gane ita ce ke neman kai ni ƙasa, har wani duhu nake gani, a haka na ƙarasa kitchen, na ci karo da kayan shayin da ya siyo na karyawar gobe, na taɓa fulas na ji akwai ruwan shayi, na kuwa juye shi a kofi, na zazzage shegiyar madarar guda ɗay wacce nake jin da ita gara babu, na juye sugan, na kaɗa na kafa kai, sai da na sha rabin kofin sannan na ajiye, na ɗauki biredin na matse shi don ya fi danƙo, na dinga ci ina korawa na cinye shi tass, na ajiye kofin na dafe kaina na fashe da kuka, Allah ne shaidata na gaji da auren nan, amma wane ne zai fahimce ni? Na bawa kaina amsa da faɗin babu, babu wanda zai gane ya cece ni sai bayan raina, amma ina fatan ko bayan raina a gene ga baƙincin da ya kashe ni, domin ya zama izina ga iyayen da ba sa bincike a kan matsalar gidan auren 'ya'yansu, Kodayake ni ce na yi wa kaina lambar da dole Baba ba zai sake yarda da ni ba, shi yasa duk runtsi ake so ka yi ƙoƙari a sanka a mutumin kirki, ko a gaba ka kuskure za a ce ƙaddara ce ko tsautsayi, ni kam na zubar da wannan damar. Banɗaki na shiga don yin wanka, sai na ga jini kaɗan ya biyo bayan fitsari, gabana ya faɗi na fara jin tsoron kar wani abu ya samu cikina, haka na yi wanka jikina har yanzu bai daina karkarwa ba, falo na koma na kwanta, na daɗe kafin bacci ya ɗauke ni, cikin baccin na farka da ciwon mara amma bai yi tsanani ba, na ji fitsari na je na yi na sake ganin jini kaɗan, na koma na kwanta, na daɗe ban koma bacci ba, ina tunanin gobe dole zan je asibiti, da kuma ta yadda zan faɗa masa zan je ɗin, saboda ba ni da kuɗi kwata-kwata, babu komai a cikin account ɗina, wannan tunanin da fargaba shi ya ɗauke ni tsayin lokaci, ina jin lokacin da ya fito ya yi alwala hakan ya tabbatar ƙarfe uku ta yi, ban dai samu bacci ba sai bayan an yi kiran sallar asuba na farko, sai a lokacin bacci ya ɗauke ni, ban sani ba ko ya tashe ni sallar asuba, ko ya tashe ni ni dai ban ji ba, don bacci ya yi min nauyi, jin mutum a jikina ne ya farkar da ni, na kalle shi cikin duhun asubar, babu kaya a cikinsa, na lura daga jiya zuwa yau ya ƙaro wulaƙanci, to ban da wulaƙanci a kan me zai dinga yin tsirara yana ƙara tsorata ni?Ƙoƙarin fizgewa nake yi don na tashi, na tuna ban yi sallar asuba ba, amma ya riƙe ni gam, ya ɗauke ni zuwa ɗakin gado, baƙinciki na kasa cewa komai, har ya sada ni da gadon ya fara yin yadda ya so, yau tsananin azaba da na dinga ji ta fi ta koyaushe, marata ta dinga ciwo, ina ture shi ya ƙi turuwa, cikin kuka na ce"Ka rabu da ni sallah zan yi, idan na yi sai na dawo ka kashe ni, dama ai ka gama kashe min rayuwa, ka kashe ni a matsayin mace, ina tafe ne gawa, ka rabu da ni". Kamar wanda ake zugawa ya ki saurarata, sai da na ce"Allah Kana kallo, Allah kai ne adalin sarki, Ka ɗora alhakin sallar da ban yi ba a kan wannan azzalumin bawan naka". Kalamaina sun yi tasiri a kansa, don haka ya rabu da ni, yana cewa"Haƙiƙa ban yi dacen matar aure ba, Allah Ya sani Assayyada kina cutar da ni, Ya Allah na yafewa matata Assayyada, kar ka kama ta da laifin hana ni hakkina na wannan lokacin". Ban bi ta kan shi ba, na tashi kafaɗa tana harɗewa na bar ɗakin, marata a ƙulle, na yi banɗaki, ina tsugunnawa jini ya fara zuba, a yanzu kam na saddaƙar cikin jikina da nake matuƙar so yana cikin haɗarin barin muhallinsa, haka na yi wankan jikina duk babu ƙwari, na fito na yi sallah a zaune, na ɓingire a sallayar ina ta kuka. Can da gari ya yi haske, ina nan a sallayar ina murƙususun ciwon mara, ya shigo ɗakin kamar an jefo shi, ya ce"Subhanallah! Assayyada". Na yi zaton ganin halin da nake ciki ne ya saka shi yin subhanallah, sai ji na yi ya ce"Assayyada, ina abun karyawata? Kar dai ki ce min kin dafa shayin kin juye suga har na naira ɗari kin shanye, sannan na ga ledar biredi, me hakan yake nufi?" Na yi banza da shi, ya ce"Wato ba lura akwai raini azeem da ya shiga tsakanina da ke a 'yan kwanakin nan, shin me kike nufi ne?" Nan ma dai ban kula shi ba, ya ce"Kaico! Kaiconki Sayyada, tirr da macen da take wofantar da mijinta, hakika ina jiye miki azabar Allah, don haka na yafe miki, komai za ki yi ki je ki yi, sai dai ki sani ni ba bawanki ba ne da zan dinga yi miki girki da sauran hidimomin gida, daga yau na janye duk wani tallafi a gareki hakkina kuma dole ki ba ni, ba zan san kina cikin damuwa da baƙinciki ba ai sai kin mutu, har ni mace za ta dinga yi wa wannan raini azeemi? Da kin san matan da suke bi na da kalmar so, da burin na aure su wallahi da tuni kin shiga hankalinki, da kin gane ni'imar da Allah ya yi miki, ki je ki tambaya mata da yawa suna can a gidajen aure cikin wani hali, saboda sun auri lusaran maza masu sharɓar bacci cikin dare, inda su ne suka samu mai wannan ni'ima irin tawa da har goya ni za su dinga yi, amma shikenan, idan ba ki godewa ni'imar Allah ba gaba za ki godewa azabarsa, zan fita, wannan ɗari biyu da hamsin ɗib da na umarce ki ki siyo kayan miya kika ƙi, yau sai ki siyo da ita, idan ba haka ba kuma ki zauna da yunwa". Ya fice daga ɗakin, ina jin fitarsa daga gidan, so nake yi na yi kuka amma ya ƙi zuwa, sai azabar ƙunci da yake rugurguzar zuciyata. Bai daɗe da fita ba jini ya ɓalle min sosai, azabar ciwon mara ta ƙaru, na dinga juyi ina kiran Allah, da tuba a gare shi, sarai na san cikin jikina ne ya lalace yake neman hanyar fita, wata zuciyar tana faɗa min na kunna wayata na kira shi, ko na kira Mama, wata zuciyar kuma tana tuna min wace ce ni a yanzu, ni ba kowa ba ce face mara 'yancin da aka aure ni saboda na zama baiwar da za a dinga kwanciya da ni babu dare babu rana, mene ne amfanin rayuwata? Gara na mutu kawai na huta, har kalmar shahada na dinga karantowa, amma ita mutuwa lokaci ne, kuma lokacina bai yi ba, a hankali na fara jin sassaucin ciwon, sakamakon fitowar halittar gabaɗaya, na kalli yadda na yi kaca-kaca a cikin jini, haka na tashi jiki babu ƙwari na gyara jikina, sannan na gyara wajen, a yadda nake jin kaina dai kamar babu komai a cikina, amma ina tuna wata ƙawata da ta ce ta yi ɓarin ciki a gida ba ta je asibiti ba, ashe bai gama zubewa duka ba, silar haka daga baya ta samu matsala sosai, kamar za ta mutu, don haka na ji tsoron, na ga dacewar zuwa asibiti, Mama ya kamata na kira na sanarwa, amma idan na kira ta tamkar a kunnen Baba na faɗa, ni kuma ba na so Baba ya sake jin wani ƙorafi daga gare ni, gara kawai ya ga gawata, don haka na fara tunanin kiran Anisa, wata zuciyar ta ce min ai daɗi za ta ji, tun da ba ta farin ciki da rufin asirinki, take na fasa, na ɗauki wayata na kunna, na san san babu komai a account ɗina, sai ko naira ɗari huɗu idan ban manta ba, amma haka dai na duba kuɗin ciki, kwatsam sai na ga ina da kuɗi a ciki har kimanin dubu ɗari shida, gabana ya ba da rass, ni kuɗu mai yawan wannan bai ma taɓa shiga account ɗina ba, to wannan kuɗin daga ina? Da yake ina da kati sai na sayi data na shiga App ɗin bankin, da na duba transaction sai na gane ta P.O.S aka tura kuɗin, na fara tunanin ko wane ne wannan tabbas mistake ya yi ba ni ya zo turawa ba, na shiga na duba massages ɗin kan waya, sai na saƙo da sabuwar lamba, bayan sallama aka rubut"Sayyada ga kuɗinki nan, ba na son ajiyar kuɗin wani a hannuna, kuɗinki ne ke kaɗai, ki yi amfani da shi hankali kwance". Kaina ya kulle na shiga tunanin wanda yake son wasa da hankalina, na kira lambar na ji layin sam ba ya tafiya ma, na yi tsuru-tsuru, wata zuciyar tana ce min tun da ina cikin buƙatar kuɗi na ci kuɗin nan kawai Allah ne Ya ba ni, wata zuciyar kuma tana hana ni, ba ni da wata mafita, don haka na saka hijjabi na ɗauki ATM ɗina na fita, jikina babu ƙwari Sam nake yin komai, ga yunwa da ta addabe ni, ga mara da cikina sam babu daɗi, kafata sai ciwo take, kada ma cinyata ta ji labari, don na fara tunanin ƙasusuwan ƙugun Ustaz ko bayan mun rabu sai sun nakasa min cinyata. Dubu ashirin na cira, na hau adaidaitasahun na tafi asibiti, ina tafe a harabar asibitin da ƙyar nake ɗaga ƙafata, ban yi aune ba jiri ya kwashe ni, na faɗi, na dai ji lokacin da na tafi luuuu zan kai ƙasa, sannan na ji salatin mutanen dake wajen, daga nan kuma ban sake jin komai ba. (Saboda na mutu😭) Prank ne kar ku tsire ni🤭 [14/10, 5:44 pm] Sadiya Abdulrazak: 21 Allah Ya taimaka akwai ma'aikatan asibitin a kusa, don haka ba a samu wanda ya sace wayarta ba, aka kwashe ta aka ba ta gado aka fara ba ta taimakon gaggawa, sannan aka ciro wayarta daga jaka, aka ɗora hannunta, fingerprint ya fita, ba a gane lambar mijinta ba, don da Malam ta yi saving, sai aka kira ta Baba, aka sanar masa asibitin da take, Baba duk ya ruɗe ga shi ba ya kusa ya je can ƙauyensu zai yi kwana biyu, da sauri ya kira Mama ya sanar da ita asibitin ya ce ta je ta ga jikin, sannan ya kira Ustaz. Ustaz yana kasuwa aiki yake amma hankalinsa yana can wajen Sayyada, tunanin wannan minus one ɗin da ya yi kawai yake yi, ji yake ya cuci kansa kamar ba zai iya jurewa ba, sai ga kiran Baba ya shigo, ya san Baban ba ya garin tun da ya faɗa masa zai yi tafiya, ya ɗaga ya gaishe shi, Baba bai ja gaisuwar ba ya ce"Malam Ashiru kana ina ne? Me yake damun Sayyada aka bar ta ta tafi asibiti ita kaɗai babu ɗan rakiya?" Ustaz ya rikice ya ce"Subhanallah! Ita Assayyadar ce ta fita daga gidan ba tare da izinina ba? To a iya sanina dai na ba ta kuɗin siyan kayan miya, ƙila ta fita za ta siyo ne". Baba ya ce"Duka fa ba wannan ba, ni hukumar asibiti ne suka kira ni, suna kyautata zaton Sayyada ganin likita ta je, shi ne ta faɗi a harabar asibitin kafin ta kai ga ganin likitan, Allah Ya taimaka ta fita da wayarta shi ne aka kira ni". Ustaz ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Ita kuwa Assayyada me ta je yi asibiti? Wallahi Baba ban san ba ta da lafiya ba, kuma ba ta ce min za ta je asibiti ba, kaico! Ni ban san me take nufi ba, ban san me ta ɗauki lamarin aure ba, amma babu komai na yafe mata, sai dai Baba ku dinga tuna mata haɗuwarta da Allah, idan ni na yafe mata Allah fa?" Baba da ransa ya fara ɓaci da wannan surutun nasa ya ce"Yanzu za ka je asibitin ne ko kuwa? Ni ma gani nan xan hau mota na taho". Ya faɗa masa asibitin da take, ya kashe wayar, a ransa yana tunanin me yake damun Sayyada da ba ta sanarwa mijinta ba? Nan take ya gasgata lallai Sayyada ba zaman lafiya take yi da mijinta ba, tun da har za ta iya fita ba ta tambaye shi ba, sannan ban da baƙin hali da ɗaukar miji ba a bakin komai ba, a ce ba ka da lafiya ba za ka faɗawa wanda kuke kwana tare ku tashi tare ba? Nan take ransa ya ɓaci, duk da ya damu da rashin lafiyar nata. Mama da ta ƙarasa asibitin ta ga halin da Sayyada take ciki ta dinga share hawaye, musamman bayan farfaɗowarta da ta faɗi cewar ɓarin ciki ta yi, ta ji tausayinta sosai, sannan ta ga ta sake rama a kan ranar da ta je gida, Mama ce take ta ɗawainiyar asibitin, da kuɗin da aka samu a jakar Sayyadar, a tunaninta ma mijinta ne ya ba ta, yanzu halin da ake ciki an ce ana so a ƙara mata jini ko leda ɗaya ne, don haka Mama ta sake kiran Baba, ya ɗaga yana tambaya ya mai jikin, ta ce"Da sauki za a ce, amma yanzu sun ce dole sai an ƙara mata jini ko leda ɗaya ne". Ya ce"Subhanallah! Mijin nata ya ƙaraso?" Ta ce"A'a, bai zo ba". Suna gama waya sai ga Ustaz ya kira wayar Sayyada, Mama ta ɗauka ya ce mata ya ƙaraso ina zai yi? Ta faɗa masa ɓangaren da suke, sai ga shi ya taho yana ta zuba saurayi, tun a adaidaitasahu yake ta jera subhanallah, har ya ƙaraso inda Mama take, ya duƙa ya gaishe ta ta amsa, cike da jimami ya ce"Ya mai jikin namu kuma? Me ya same ta ne?" Mama ta ce"Ai na zata ka san ta yi ɓarin ciki ko? To bayan ɓarin ne ta taho ganin likita shi ne jiri ya kwashe ta ta faɗi, tsakani da Allah bai kamata a ce ka bar ta da ɗanyen jiki ta taho asibiti ita kaɗai ba, idan ma ba ka da lokacin kai ta ai ya kamata ka sanar min, ni sai na kai ta, ko na turo wata ta raka ta". Ya ce"Subhanallah! Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Wato Mama haƙiƙa na kula kamar Sayyada ba ta da lafiya kafin na fita, amma da na ga ba ta faɗa min ba ta jin daɗi ba, sai na yi zaton kawai kasala ce, bi ma'ana dai irin larurin nan na masu juna biyu, a halin yanzu ban san an rasa cikin ba sai yanzu da kike faɗa min, haƙiƙa sai bayan na fita komai ya afku, subhanallah!". Mama sam ba ya burge ta, haushin shi take ji tun da ta san hariji ne mai cutar 'yarta, don haka ta ce"Yanzu dai tana ciki, kuka jini ake buƙata za a ƙara mata ko leda ɗaya ne". Ya ce"Subhanallah, abun har ya kai haka?" Mama ta ce"Zai iya fin haka ba, don wannan ramar da take yi ba ta lafiya ba ce, daga gani ba ta cin abinci mai gina jiki". Ya ce"A yi haƙuri Mama, in sha Allahu za a fara siyo mata abubuwa masu gina jiki, akwai me zogale da kullum take zuwa kasuwarmu, in sha Allah zan daure na dinga siyo mata tana kwaɗawa, tun da a bisa bincike na masana kiwon lafiya an ce zogale ya fi kaza amfani a jikin ɗan'adam, yanzu ya jikin nata?" Ta ce"Da sauƙi za a ce, duk abin da aka buƙata na siya da kuɗin da na gani a jakarta, yanzu jinin ne dai ban san yadda za a yi ba, ai sai dai a siya". Ya ce"To ai dama ba a riga an siya ba, da sai na siya, tun da hakkina ne, bai kamata a ɗauke min nauyina ba, amma tun da an riga an siya la ba'asa, na gode". Mama ta ce"To ai ga siyan jini nan a gaba". Ustaz ya sauke numfashi, shi fa fitar da kuɗin siyan jinin ne yake jinjinawa, shiyasa ma ya ga kawai gara a ɗibi nashi a saka mata, kuɗinsa ya huta, idan ya siya zogale na ɗari biyu maltina guda ɗaya ya san zai mayar da jininsa ai, don haka ya ce"Subhanallah! Mama da raina da lafiyata ai ba zai yiwu na zuba ido a ce wai a siya jinin da za a ƙarawa matata ba, nawa za a ɗiba a ƙara mata in sha Allah". Mama ta kalli yadda yake a bushe sai tsayi kamar daren mutuwa, gani take jinin jikinsa bai kai ma leda ɗaya ba, amma shi ne yake cewa a ɗibi na shi". Kafin ta ba shi amsa likita ya ƙaraso inda suke, ya ce da Mama wai kun gama yanke zancen jinin kuwa? Yana da kyau a saka mata". Mama ta ce"Ga mijinta nan, ya ce a ɗibi nashi". Likitan ya yi masa kallon sama da ƙasa, ustaz ya jinjina kai ya ce"Na'am in sha Allah!" Likita ya miƙa masa hannu suka yi musabaha, sannan ya ce"Amma Malam anya za a samu a jikinka kuwa?" Ustaz ya yi murmushi ya ce"In sha Allah, ai ko ba za a samu yadda ake so ba, indai an samu ledar da za a sakawa ita Assayyadar to a ɗiba a saka mata, domin ni fa ba zan ɓoye muku ba, kishina ba zai bari a ce an ɗauki jinin wani ƙato an sakawa matata, ya dinga gudana a jikinta ba, don haka dole nawa za a ɗiba". Likitan ya sauke ajiyar zuciya ya ce"To babu damuwa, mu je lap sai a ɗiba a gwada, idan zai yi ba matsala sai a ɗiba ɗin". Ya ce"In sha Allahu zai yi, lafiya ƙalau ne". Suka je aka gwada gabansa sai faɗuwa yake yi, aka ga zai yi daidai da na Sayyada, sai dai shi kansa jinin jikinsa ya yi ƙaranci, inda za a ƙara masa yana buƙata, don haka likitan ya ce"Malam sai dai fa ka yi haƙuri, level ɗin jininka bai kai wanda za ka iya ba wa wani gudunmawa ba, domin kai ma kana buƙata". Ustaz kamar zai yi kuka ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Kun dai rantse sai kun gurɓata jinin matata da na wani gardin da ban san ma wane ne ba, likita ka dubi girman Allah ka ɗibi jinin nan nawa, a saka wa matata halattaccen jinin mijinta, wallahi idan aka saka mata jinin da ba nawa ba zan iya haɗiyar zuciya na mutu don kishi". Ya ce"Idan aka diba fa za a iya samun matsala". Ya ce"Haba likita, kar fa ka manta fankam-fankam ba ta kilishi, ba wai don ka gan ni babu ƙiba bane zai tabbatar maka ni ba namijin duniya ba ne, wallahi ko zan mutu na yarda na sadaukar, ka ɗiba kawai". Aka ja leda ɗaya, aka bar shi kwance yana hutawa, aka je aka sakawa Sayyada. Bacci ya kwashe Ustaz, zuwa azhar ya tashi, ya ji an shiga sallah a masallacin asibitin, ya ce"Subhanallah! Alhamdu billahillazi ahyana, ba'ada ma amatana, wa ilaihinnushur". Ya yunƙura ya tashi, jikinsa duk babu ƙwari, sai yake ganin duhu-duhu tamkar duhun magriba, ya ɗauki wayarsa dake gefen gadon ya danna, ya ga ƙarfe biyu saura, ya ce"To ya aka yi na ga garin duhu? Ko dai dare biyu za a yi? Subhanallah da alama yau ana kusuf al shams, bi ma'ana rana tana rashin lafiya, ya zama dole na yi sallar da ake yi yayin faruwar haka". Ya sauke daga gadon, yana miƙewa tsaye ya ga duhun ya ƙaru, kansa ya fara juyawa, ɗakin duka juya masa yake yi, yana ta ƙoƙarin laluben bango ya dafa shi ya fake, amma ya ji kamar wan yi sama da shi an maka shi da ƙasa, ji kake yifff, daidai lokacin kuma Baba ya shigo ɗakin don ganin jikin nasa, kawai ya gan shi wanwar a ƙasa, Baba ya fara salati ya fita da sauri ya kira likita, aka kwashi Ustaz aka mayar gadon, likitan yana mita da faɗin dama ya san za a iya yin haka, ƙarshe dai Ustaz sai da aka ƙara masa jini leda biyu, da na yayansa da na ƙaninsa, don Baba wayarsa ya ɗauka ya duba lambar mahaifinsa ya sanar da shi. Lokacin ita Sayyada ta dawo normal, amma sai kuka take yi na rasa ɗanta a karo na biyu, Mama duk ta damu ta ce"Sayyada ko dai da laifin mijinki a zubewar cikin nan?" Sayyada ta kalli Baba, sai ta girgiza kai ta ce"Babu, Allah ne ya ƙaddara". Mama ta ce"A'a Sayyada na san halin mutum hariji..." "Saboda kin zauna da shi ko?" Baba ya katse ta da faɗin haka yana haɗe rai. Ya ɗora da faɗin"Shikenan ciki ba zai zube ba idan Allah Ya ƙaddara? Duk matan da suke ɓarin ciki mazajensu harijai ne kenan? Kalmar hariji ta fita daga bakinki, ba na son neman fitina". Mama ta ce"Na tabbata idan ba shi ya zubar da cikin nan ba, to baƙincikin da yake ƙunsa mata ne, don haka wannan karon ba za ta koma ba". Na share hawaye na ce"Mama zan koma, in sha Allah ba zan sake yin yaji ba, zan zauna na jure komai, idan kun ga na gaza to na mutu ne, ka kwantar da hankalinka Baba, na yi alƙawarin ba zan sake kawo ƙarar mijina ba, zan zauna da shi a yadda yake, roƙona ɗaya kawai shi ne Baba ka dubi azabar da nake ciki da sunan aure, ka yafe min bayan mutuwata". Jikin Baba ya yi sanyi, amma ya dake bai ce komai ba ya fita ya bar ɗakin. Mama ta ce"A'a Sayyada na za ki koma ba, wallahi ba za ki kashe kanki ba, daga nan gida za ki koma". Na ce"A'a Mama daga nan gidana zan koma in sha Allah, ki taya ni Baba ya aminta da ni". Mama ta ce"Amincewar Allah kawai za ki nema Sayyada ba ta mutum ba". Na ce"Ta shi ɗin ma ina buƙata". Mama ta ce"Ba za ki iya ba Sayyada". Na yi murmushi mai ciwo hawaye bai bar zuba ba na ce"Zan iya in sha Allah, sai dai gawata ta faɗa muku na gaji ba dai ni da bakina ba". Ustaz yana kwance hajaran majaran, ido ya yi zuru-zuru, don ma ya ci faten wake mai alayyahu da kifi, sannan ya sha maltina da madara, ya sha fruit,kana kallonsa ka san yana jin jiki amma don ƙarfin hali faɗi yake"Alhamdulillah, ko mutuwa na yi ba ni da kaico, tun da kamar jihadi ne na yi, bi ma'ana na kare matata daga gudanuwar jinin wani ƙato a jikinta, Alhamdulillah!" Da Baba ya ce da Sayyada tun da nata jikin da kwari ta je ta duba jikin mijinta, haka ta je ba don ranta ya so ba, ta yi masa sannu, ya amsa shi ma yana yi mata sannu, zai fara yi mata surutu ta fice daga ɗakin, a asibitin dai suka kwana, washegari aka sallame su, Mama ta yi, ta yi Sayyada ta zo su tafi gida sai jikinta ya ƙara kwari, amma ta ƙi, shi kuma Baba ya fa faɗan da gaske Mama ce take so ta kashe mata aure, a dole ta koya mata yadda za ta dinga kula da jikinta, sannan ta ce za ta dinga zuwa tana duba ta, suka rankaya ita da Ustaz suka tafi gida. Ustaz fa ya narke da gaske har lokacin jikinsa bai dawo daidai ba, ga shi an ce dole shi da Sayyadar su dinga cin abinci mai gina jiki, haka ya lallaɓa ya je ya yi musu cefanen kayan miya, har da alayyahu da kifi, ya zo ya ajiye a kitchen, ya shigo falon da nake a kwance ya ce"Assayyada, daure ki fito ki ɗora mana abinci, ga shi nan na siyo har da kifi". Na tashi na fita, na shiga kitchen ɗin, na buɗe ledar na yi zaton zan ga ɗanyen kifi, kawai sai na ga soyayye ne, irin ƙawarar nan mai ƙaya a jikinsa, ya ƙaraso kitchen ɗin ya ce"To kin ga kifin da aka samu, sai a ƙarshen girkin za ki saka shi, bi ma'ana idan abincin ya ɗakko tsotsewa, sai ki zuba shi a ciki ki juya, ai ina ga ma tun da ga alayyahu nan za ki cika a abincin, shinkafar sai ki dafa gwangwani biyu da rabi maimakon uku da ake dafawa, tun da ba lafiya gare mu ba". Ko kallon shi ban yi ba, na hau gyara kayan miyan, gwangwani biyar na dafa a maimakon huɗu, na cika masa faranti kuma ya cinye tass, ni kuma na ci kaɗan, don bakina babu tes, na sha magani na yi sallah na kwanta, da yamma Anisa ta zo ta duba ni har da yo min jar miya mai yawa, mai cike da nama, da kuma gasasshen nama cikin 'yar kula, na karɓa kadaran kadahan, tana zuwa ya fita, kuma har ta tafi bai dawo ba, tana tafiya ni ma na saka hijjabi na fita, na je na ciri kuɗi, na sayi kayan shayi manyan gwangwani, maltina katan ɗaya, ƙwai, cornflakes, golden morn, suga, da babban biredi da butter, indomi kwali ɗaya, don ba zan bari ya kashe ni da yunwa ba, kuɗin nan kuma ko ma wane ne ya turo min, ko mene ne manufarsa ta ba ni kuɗin ni dai ci zan yi, tun da ina da buƙata. Da na ga na mallaki wannan kayan shikenan ba na yi masa girki, ko ya yi ko ya siyo a waje, ni kuma idan ba ya nan zan fita na siyo alayyahu da kifi ko nama na yi girkina iya cikina na ci na yi wanke-wanke don kar ya gane. Kwana biyu da dawowarmu daga asibiti, ya fara nuna rashin haƙurinsa, haka zai yi ta naniƙata yana tumirmushe ni da sunan samawa kansa nutsuwa, ni kuwa har ba na fatan ma na samu tsarki nan kusa. [15/10, 7:17 pm] Sadiya Abdulrazak: 22 Wani irin zama muke yi da shi, babu gaisuwa, idan ya yi min magana sai wacce na ga dama zan amsa, saboda sosai nake jin tsanar shi a zuciyata, kullum sai ya yi mini nasiha da wa'azi mai tsoratarwa a kan wannan abin da nake yi masa wulaƙanci ne, haka kullum sai ya tambaye ni ko na samu tsarki? Ba na kula shi, sai dai idan yana samawa kansa nutsuwa ya taɓa ya ji, sai ya ce"Subhanallah! Allah Ya kawo mana ƙarshen abun nan". Kwana na takwas da zubewar cikin jinin ya ɗauke na yi tsarki, ranar na makara sallar asuba, bai tashe ni ba saboda bai yi zaton na fara sallah ba, ina tada sallar ya dawo daga masallaci, ya yi turus, sai kuma ya fara murmushi ya ce"Alhamdulillah! Ma sha Allah!". Ya tuɓe ya zauna a bakin gado yana jira na idar, ina idarwa ya ce"Assayyadata". Ban kalle shi ba ballantana na amsa, ya fara girgiza kai alamar jimami kafin ya yi gyaran murya ya ce"Subhanallah! Kaico! Kaicon mutanen da suka shagala da ruɗin wannan zamani, kaico da nasara da ya kawo mana abubuwan da suke canza al'ada wasu har ma suke taɓa addini, yanzu Assayyada dama kin yi tsarki, kin zama tsarkakkiya kuma halattaciya a gare ni amma shi ne kika ƙi sanar da ni? Mu fa ba turawa ba ne, mu musulmai ne, ke kin san babu abin da nake jira a 'yan kwanakin nan kamar a ce kin samu wannan tsarki, amma kika yi biris kika bar ni a wahale, a jigace, a raunace?" Idona ya kawo ruwa, amma ban bari ƙwallar ta sakko ba, na shiga ƙarfafar kaina da cewar na daina yin kuka a kan lamarin aurena. Mama ta kawo min maganin sanyi, da na ƙarin ni'ima, amma suna nan ban taɓa ko ɗaya ba, a ganina gyara jikinsa tamkar ƙara zuga shi ne ya sake maƙale min, gara na zauna a yadda nake ko Allah zai sa ya ga canjin ya yi yawa ya ja baya da ni. Ya ce"Hmm, shikenan na yafe miki, sai dai kuma ya za ki yi da alhakina da kika ɗauka?" Ya taso ya ɗaga ni tsaye, yana kallon fuskata, na sunkuyar da kai baƙinciki kamar zai kashe ni, ya ce"Assayyadda ni mijinki ne, kuma wannan haƙƙina ne dole ki ba ni ko ba kya so, sannan ina jiye miki zuwan ranar kuka, bi ma'ana ranar da turar da kike yi min za ta kai bango, har zuciya ta ci galaba a kaina na aikata abin da ba shi Kenan ba, wallahi Assayyadda sai ƙaddara ta saka kin auri wani za ki gane ashe ni ɗan baiwa ne kuma Allah yana sonki da ya na ki ni a matsayin miji". Ganin dai ba zan kula shi ba, ya shiga raba ni da suturar jikina, yana yi yana tasbihi kamar yadda ya saba, ya gama ya ja ni zuwa gadon. Ni kaina na san ba ni da ni'ima sosai, rabona da shan wani abu da sunan gyara jikina tun kafin na tare, tun da na san wa na aura na ga cewar shan magani ba nawa ba ne, duk da na san cewar yawan ni'imar zai kawo min sassauci, idan ya daɗe yana abu ɗaya, kuma wasu suna cewa idan ni'ima ta yi yawa namiji yana saurin samun gamsuwa, amma ina baƙicikin ya ji daɗik ya sa ina jin ba zan taɓa shan wani abu ba, na san sarai a buɗe nake, irin buɗewar da nake buƙatar matsi duk da ban taɓa haihuwa ba, to amma idan na gyara ma ai na yi banza, tun da lokaci ƙalilan zan sake buɗewa. Na sha wahala sosai, zafin abun kawai nake ji, gani nake ko Allah Ya raba ni da shi kafin na mutu, to idan na yi wani auren sha'awata ba za ta dawo ba, saboda ya kashe ta murus, yau duk yadda na gaji ban ture shi ba, zuciyata dai tana ta zafi kamar zan mutu, sai da ya gama don kansa, lokacin gari ya waye, sannan ya koma gefe, a bazata na ji maganarsa ya ce"Allah wadaran naka ya lalace". Na yi mamakin maganar, amma na shanye mamakin, na sauka daga gadon, da na yi wanka, kaya kawai na koma na ɗauka a ɗakin na koma falo na kwanta, ina jin kaina yana ciwo, da alama ya saba da kin yin girkina, yana yin wanka ya shiga kitchen, sarai na san gas ya ƙare, ina sane ban faɗa masa ba, babu jimawa sai ga shi ya shigo yana muzurai yana faɗin"Assayada, wai da me kike taƙama ne? Shin ba kya tunanin zuwan yaumu tubulas sara'ir? Idan mutuwa ta riske ki a wannan baƙin halin da kike nunawa mijinki me za ki ce da Allah?" Zuwa yanzu maganganunsa sun daina firgita ni, don haka ko kallonsa ban yi ba, ya ɗora da faɗin"La ba'asa, na gano dalilin, wato ainafin kuskure na yi babba da ban ajiye miki gawayi ba, na bar ki har yanzu kina girki da gas, duk ƙoƙarin nan da na yi banki gani ba sai kin ƙure ni? A ce gas din ya ƙare ƙi ƙi sanar da ni sai yanzu da nake shirin na dafa abin da zan sakawa bakin salati na tafi neman halal?" Sai ya koma ɗakin gadon, ya dawo ɗauke da wayarsa yana cewa"La budda laifina ne". Ya zauna a kujerar nesa da ni, ya yi danne-danne a wayar ya kar a kunne, babu jimawa na ji yana"Assalamu alaikum, Baba barka da safiya". Gabana ya ba da rass, suka gaisa, ya ce"Wato Baba dama wani lamari ne yake faruwa a nan gidan namu, tun da Sayyada ta dawo daga asibiti sau ɗaya ta yi girki a gidan nan, shi ma ina kyautata zaton ta yi ne saboda ta ga kifi a cikin cefanen, to Baba a ce Shikenan ko ba ni da kuɗi sai na siyo kifi kullum za ta yi girki? Ta daina girki ta daina gaishe ni, dau na yi mata magana sau dubu ba za ta kalle ni ba, rayuwar aure za ta yiwu a haka? Duk haƙurina Sayyada ta fara kai ni bango, don Allah Baba idan kun isa da ita s daure a yi mata magana ko za ta ji, duk da dai ni na yafe mata ma". Ban ji me Baba yake cewa ba, amma na ji Ustaz yana ta ba shi haƙuri yana ce masa ai ya yafe min, amma dai a yi min magana. Ya gama wayar ya kalle ni ya ce"To bari mu ga kina jin maganar iyayenki ko kuwa rafkanar ta ki ta saka har iyayen ma ba su da wannan tasirin?" Ya fita ya bar ɗakin, na san wayata a kashe take, kuma ina sane yanzu Baba yana can yana kirana, amma na ƙi kunna wayar, sai ga Ustaz ya dawo ya miƙo min wayar, na karɓa na kara a kunne na yi sallama, na gaishe shi, ya amsa ya dora da faɗin"Sayyada me yake damunki ne?" Na ce"Baba babu komai". Ya ce"To wani sabon wulaƙancin ne kika tsiro da shi haka wanda za ki dinga mayar da mijinki ba a bakin komai ba?" Na yi shiru, ya ce "Ba magana nake yi miki ba? Ko wani laifin ya yi miki?" Na ce"Bai yi min komai ba". Ya ce"To akan me kika canza kika tsiro da wannan wulaƙanci?" Na ce"A yi haƙuri Baba, zan gyara". Ya ce"Maza ki ba shi haƙuri, kuma kar na sake jin irin wannan ƙorafin daga mijinki, don kina zubar da ƙimar gidanmu ne". Na ce"To, a yi haƙuri". Na miƙa masa wayar ina kallon gefe na ce"Ka yi haƙuri". Ya ce"Subhanallah! Assayyada anya kuwa kina tuna sai na ɗaga ƙafata za ki shiga aljanna? A hala za ki ba ni haƙuri ba za ki duƙursa ba? Ni fa mijinki ne? Gaskiya da gyara a lamarinki, sai kuma na yi zancen ƙara aure ki ce za ki tada kishi, shiriritar banza kenan, yanzu kin ji maganar tasa ko kuwa da saura?" Na ce"Na ji". Ya fita daga gidan, sai ga shi ya dawo da leda, shayi ne ya siyo shi a leda ƙulli biyu, sai biredi kamar wanda ya saba siya, ya zuba nashi a kofi ya bar min sauran, na ce"Ka haɗa ka shanye ni ba sha zan yi ba". Ya ce"Hmm! Assayyadda kenan". Ya gama abinda zai yi ya fita kasuwa, sai lokacin ma tashi na zubo ruwan zafina dake cikin fulas na haɗa shayi na sha, na share gidan, na fita na siyo maganin ciwon kai, na yi cefanena, wajen sha biyu na rana sai ga shi ya zo da murhun gawayi, da kuma gawayin ƙulli biyu, da taliya leda ɗaya sai kayan miya, ya ce"Ga wannan, ina ga gas ɗin nan sai ki matsar da shi gefe, saboda halin rayuwa, a koma amfani da gawayi kawai". Ban ce komai ba, na kunna gawayin, zan fara gyara kayan miya ya kwala min kira, kamar na yi banza da shi, sai kuma na tuna umarnin Baba zan bi ba nashi ba, don haka na je, na tarar da shi babu kaya, yana miƙo min hannu, na kau da kai ban yi magana ba, kuma ban ƙarasa ba, ya ce"Taho mana Assayyadda, gafin gawayin ya kama, sai a toshe wani wajen". Na kasa yin ko taku ɗaya ballantana na je, sai shi ne ya zo ya ja ni zuwa gadon, duk azabar da nake ji haka na daure ban hana shi ba, fata nake yi wahala ta kashe ni kawai, kiran sallar sha biyu da rabi ne ya cece ni, ya fara faɗin "Subhanallah! Ba kya tuna min kin kunna gawayi?" Ya fita yana cewa"La haula wa la ƙuwwata illa billah, kin ga yanzu ga shi an yi asarar rabin gawayin, wato ainafin ya fara zama toka". Ya fito daga banɗakin, ni ma na shiga, ina fitowa na ɗauki ɗayan ƙullin gawayin zan ƙara, daidai sanda ya fito daga ɗaki, ya ce"Lala-lala, kul Assayyadda, wannan ai na gobe ne, ki fifita ki ɗora a haka, ai tun da taliya ce tana saurin dahuwa". Na ajiye, na gyara kayan miya, na ɗora tukunyar, ya ce"To sai ki kula wajen tsayar da sanwar, taliyar za ki dafa biyu bisa uku ne, bi ma'ana ki raba ta gida uku, sai a ajiye kashi ɗaya gobe da safe idan Allah Ya sa muna cikin rayayyu kuma lafiyayyu sai mu dafa mu karya da ita". Ya tafi masallaci, yana dawowa ya shuga ɗaki ya kwanta, ban shiga ɗakin ba sai da na gama dafawa, kamar yadda na yi zato bacci ne ya kwashe shi, ko wannan rashin samun wadataccen baccin ba zai bar shi ya yi ƙiba ba, na ajiye masa abincin, ban tashe shi ba, na yi alwala na tada sallah, na idar ina zaune a sallayar ya farka, ya fara ƙorafin me ya sa ban tashe shi ba, ya ce na zo mu ci abincin, nan ma ban kalle shi ba, ya cinye tass sannan ta hau tambaya ta gida ukun na raba? Ban ba shi amsa ba, ya fice daga gidan yana cewa"Allahu yahdiki Assayyadda". Dab da magriba na fita bakin titi na siyo tsire da yogurt, na ci na ƙoshi, da daddare da ya dawo na ba shi sauran taliyarsa, ya cinye tass, ga shi dai daga rana zuwa dare shi kaɗai ya cinye leda ɗaya, amma saboda son zuciya ya ce mu biyu ma ba za mu ci leda ɗaya ba, bai gaji ba da daren ma ana yin sallar isha'i ya ja ni zuwa ɗaki, yana cewa"Ɗan karatun ma kin daina kin watsar, tun da irin wannan karatun kawai kike so ai sai mu yi ta yi". Tun daga ranar nake yin girki safe da rana, wataran na yi nawa da ban, wataran kuma na siyo nama na yi miya idan na yi girkin sai na ci nawa da miyata, yawan ciwon kai da nake yi yana damuna, yanzu har na gaji da shan maganin, sai na ji ya yi tsanani sosai nake sha, na kashe wayata, don ba iya media ba duka duniyar ma kawai ji nake ta ishe ni, ga ciwon ƙirji da nake ji kaɗan-kaɗan, duk da ba ni da ulser, ni kaina na san ina buƙatar ganin likita, idan na yi tunanin zuwa asibiti sai na ga me na zan je na yi? Ni da so nake ma na mutu? Sai na fasa zuwa, a yanzu tsakanina da Ustaz ya ba ni umarni ne kawai na aiwatar, sai na yi kwana uku cif ban furta masa kalma ɗaya ba, ban da karatun sallah fa ba na buɗe baki da nufin yin magana, abincin ma na rage ci, ba na wani sha'awar cin komai, ina ci ne don maganin yunwa. Ko da makaho nake zaune dole zai gane ina cikin damuwa mai tsanani, amma Ustaz kamar bai gane ba, kawai ba shi da wani buri sai na kwanciya da ni ya biya buƙatarsa. A hankali abubuwa suke ƙara ta'azzara, yanzu sai na yi kwana uku ban yi wanka ba, kayana duk sun yi datti ban wanke ba, idan na zauna ba ni da aikin yi sai tunani, tunanin da yake ƙara min zafin zuciya, sannan ina yawan zargin kaina, ko alwala na yi sai na ga kamar ba daidai na yi ba, sai na yi sallah na manta na yi na ƙara yi, ko kuma na dinga ganin kamar na yi, alhalin ban yi ba, ciwon kaina kuwa ya yi tsanani, ga rashin bacci, haka zan kwanta na yi ta tunani na kasa bacci, ko ya ce na tashi na yi sallah ba na yi. Tun yana banza da ni har ya fara damuwa, ya sha zaunar da ni yana tambaya ta mene ne yake damuna, amma ko kallonsa ba na yi, saboda ni ma ban san abin da yake damuna ba, a hankali kuma na fara jin jiri, wani lokacin idan ya kwashe ni sai na tsaya na dafa bango, saboda duhu nake gani, idan na dawo normal sannan na cigaba da abinda nake yi, a haka nake yin girki, amma wanke-wanke na daina yin shi yadda ya kamata, ɗaurayewa kawai nake yi, wani lokacin sai na ji kamar ana ihu a cikin kaina, ko na ji na tsani kowa, mutuwa kawai nake so, har na fara tunanin me zai hana na kashe kaina? Sai zuciya ta ce min ko zan mutu ba yanzu ba, na bari sai na haihu, na bar bayana wanda zai saka a dinga tunawa da ni. Sai na fara tunanin idan na mutu ko Ustaz zai damu? Ko wa zai aura? Ko za ta iya zama da shi? Sai kuma na tuna ko Baba zai yafe min? Wane irin kuka Mama za ta yi? Kawai sai na fashe da kuka, na yi mai isa ta babu mai rarrashi, wataran kuma sai na dinga tuna rayuwata ta baya, ta gidan Sadam, lokutan farinciki nake tunawa, wanda a da na neme su na rasa sai na baƙinciki, yanzu suna ta dawowa kaina, sai na yi murmushi, idan na tuna wani abun kuma na ƙyalƙyale da dariya, kuka ko dariya duka ina yi a gaban Ustaz, don haka ya fara tunanin ina da aljanu. Idan ina irin haka kuka ko dariya, ko kuma na zauna na ƙurawa waje ɗaya ido ya yi min magana na ƙi amsawa, sai ya yi addu'a a cikin ruwa ya zo ya dinga watsa min, yana tambayar "Su wane ne ku? Me kuka zo yi jikin matata?" Idan yana wani surutan har dariya yake ba ni, sai dai kawai na yi murmushi. Wata rana na tashi da ciwon kai mai tsanani, ko motsa kan na yi kamar na kurma ihu, ga jirin da nake ji yana kwasara, har dafa bango nake yi idan zan yi tafiya, daren jiya ban samu bacci ba ko na minti ɗaya, idona sai zafi yake yi, ina kwance a tsakar gida Ustaz ya zo kaina ya fara faɗa"Sayyada, ke Sayyada, wani sabon salon ne kuma kika samo? Yau da me za mu karya? Ki tashi ki ɗora, ko na kira mahaifinki na sanar da shi halin da ake ciki, a gaskiya na fara gajiya, 'yar nutsuwar da nake samu ma yanzu haƙuri kawai nake yi, bi ma'ana ɗanɗanon kullum raguwa yake yi, ga shi abu yana ƙara buɗewa, a gaskiya ki gyara". Haka na tashi ina dafa bango na kunna wuta na dafa masa indomi, na koma na kwanta a falo, ya karya ya fita kasuwa, wajen sha biyu ya dawo kamar yadda ya saba, ina kwance a tsakar ɗakin ina jin dawowarsa amma ba ni da ƙarfin da zan ɗago ma na kalle shi, yana ta yi min faɗan ban ɗora girki ba, na yunƙura zan tashi na kasa, ni ina ta kaina shi kuma zani na da yaye ne ya sa shi matsowa ya fara shafa cinyata, a nan tsakar ɗakin ya raba ni da kayan jikina ya shiga biyawa kansa buƙata, numfashina yana ta sama da ƙasa ina jin kamar zan mutu, har dai na samu ya gama, ya shiga banɗaki, na yi jarumtar tashi tsaye, na ji kaina ya fara juyawa kamar ana hajijiya da ni, na tafi luuuu na zube a ƙasa. Ustaz ya ji ƙarar faɗuwar Sayyada, a hanzarce ya karasa wankan, ya fito, ya same ta a wannan yanayi, ya shiga tashinta yana jijjiga ta, amma shiru, shi a tunaninsa aljanunta ne suka tashi, ya ɗakko zani ya lulluɓa mata, sannan ya yi addu'a a ruwa ya fara yayyafa mata, ya buɗe murya ya dinga yi mata karatun ruƙiyya shiru kake ji, ko motsawa ba ta yi ba. Can dai ya ɗakko waya ya kira Baba, suka gaisa ya ce"Baba wato akwai babban lamari da yake faruwa a nan gidan namu". Baba ya ji gabansa ya faɗi ya ce"Subhanallah me ya faru?" Ya ce"Wato ainafin ita Sayyada ce ta haɗu da laruri na aljanu, ina ta iya ƙoƙarina a kan lamarin, to yau dai ta faɗi, kuma na yi iya yi na na daga ilimin da Allah Ya ba ni domin na ga ta tashi ko kuma su aljanun su magantu a ji da wacce suka zo, ko kuma a ki wasu iri ne ma, farare ne ko baƙaƙe? Sannan Baba ka san su aljanu kala-kala ne, ka ga akwai Ruhanai, su an ce bayin Allah ne, sannan akwai..." Baba ya ce"Haba Malam Ashiru! Yanzu a wane hali Sayyada take?" Ya kalli Sayyadar ya ce"E to, ga ta nan dai a kwance, amma na faɗa maka na karanta Fatiha da Ayatul kursiyyu, amanarrasulu, sannan..." Baba ya ce"Ga mu nan zuwa gidan". Ya ce"To sai kun zo". Da sauri Baba ya hau adaidaitasahun, sannan ya kira Mama ya sanar da ita, kusan a tare suka ƙarasa ƙofar gidan, Ustaz ya buɗe, Mama tana shiga ɗakin ta ga Sayyada kamar gawa, ya yafe zanin da ya rufe ta, ta gan ta tsirara, nan take ta zargi saduwa ya yi da ita har ta fita hayyacinta, ta kai hannu ta buɗe ƙafarta don tabbatarwa, ai kuwa ta samu tabbacin, Ustaz ya yi saurin barin ɗakin saboda tsananin kunya yana faɗin"Subhanallah!". Ta saka mata kaya, suka kwasa suka tafi asibiti, amma ban da Ustaz, cewa ya yi bari ya nemo mukullin gidan idan ya rufe gidan zai biyo bayansu, saboda kar a tafi tare da shi a ce komai shi zai biya, amma ya san idan ya yi jinkiri, duka za su biya komai, kuma za su yafe masa tun da su ma 'yarsu ce. [16/10, 4:14 pm] Sadiya Abdulrazak: 23 A daidaitasahu, Sayyada tana kwance jikin Mama, ƙafafunta a jikin Baba, duk jikinsa ya yi sanyi, ya fara tunanin tabbas Sayyada tana matsanancin hali, ta rame duka ta ƙare kamar ba ita ba, ita kuwa Mama kuka kawai take yi tana faɗin"Ya kashe ta, ya kashe min 'ya, Allah Ya saka miki Sayyada". Baba ya ce"Don Allah ki saurara haka, yanzu da kike maganganun nan wa kike faɗawa? Ni ko mai adaidaitasahun?" Ta ce"Allah nake faɗawa, duk da na san yana gani, ƙara nake kai masa ya bi wa 'yata hakkinta". Baba ya ce"Ai shikenan, kya dai bari a je asibitin a ji me ya same ta, kafin ki ɗora laifi a kan wani". Mama ta ce"Ai da gaske? Da gaske ba ka san abin da ya same ta ba? Tsirara fa na tarar da ita, ya gama biyan buƙtarsa ya kashe ta, ka san illar zama da hariji, na faɗa maka ga halin da take ciki, amma ka ce ta je ta mutu shi ne burinka, to yau ga shi ta mutu kowa ya huta". Ta fashe da kuka sosai, har aka ƙarasa asibitin kuka take tana surutai, suna zuwa aka ba wa Sayyada gado a emargency, da kuɗi a account ɗin Baba, don haka komai ya zo da sauƙi, suka biya kuɗin komai aka duƙufa a kanta, Baba ya yi mamakin rashin ƙarasowar Malam Ashiru da wuri, kuma ransa ya ɓaci, suna nan zaune likitan da ya duba ta ya fito ya ce"Ina mijin yarinyar nan?" Baba ya ce"Bai ƙaraso ba, sai dai ni mahaifinta". Mama ta ce"Likita ya jikin nata? Ta mutu ko?" Likita ya ce"A'a ba ta mutu ba, ta farfaɗo daga saman da ta yi, ta samu bacci, in sha Allah babu damuwa sosai". Ya kalli Baba ya ce"Malam mu je office akwai bayanin da zan yi maka kafin mijin nata ya zo". Mama ma ta tashi ta bi su suka shiga tare, Likita ya fara da faɗin"To a gaskiya kun yi sakaci da lafiyar 'yarku sosai, kuma abin da bincikenmu ya ba mu a yanzu haka 'yarku tana cikin stress ne, wato ciwon damuwa, wannan ciwon ba iya a gangar jiki yake ba, ciwo ne na ƙwaƙwalwa da zuciya, faɗuwar da ta yi yanzu alamu ne da ke nuni da zuciyarta ta gaji, ta gaza ba wa gangar jikinta gudunmawar da za ta iya zama lafiya ta yi rayuwa kamar kowa, idan ba a kula an yi taka-tsan-tsan ba, wannan cutar za ta iya kai ta ga mental breakdown, a yanzu ma haka dole abun ya taɓa ƙwaƙwalwarta, sai dai za ta iya warkewa idan ta fita daga cikin ƙuncin da ya haddasa mata faruwar hakan, sannan a kula da farincikita sosai". Jikin Baba ya yi sanyi. Likita ya ɗora da faɗin, yana da kyau a ce an lura da canje-canjen da ta samu kafin faruwar haka, mutum yana zama mai yawan yin shiru, rashin cin abinci, sannan da tsoro da tsarguwa, rashin yarda da kai ma gabaɗaya, da kuma mantuwa, idan yarinyar nan ta tashi na tabbata za a ji haka ta faru da ita, sai kuma wani babban lamari da muka lura da shi, wanda shi ma zai iya kawo mata wannan faɗuwar, mun gano an sadu da ita lokaci kaɗan kafin kawo ta asibitin, idan tana cikin halin rashin lafiya hakan ta faru musamman ba da son ranta ba, ko an yi abin da ya cutar da ita, tabbas hakan zai iya tada ciwon ta yi irin wannan faduwar". Mama ta ce"Tabbas haka ta faru, ni ma na ga alamar ya sadu da ita, kuma dama hariji ne, ta ce ta gaji tun tuni, tun tana kawo kukanta har ta gaji ta daina". Likitan ya ce"To wannan shi ne babban kuskuren da kula yi, ta ya za ku ɗauki yarinya ƙarama irin wannan ku haɗa ta da wanda ya fi ƙarfinta?" Bana ya ce"A yi haƙuri Likita, ni da fari ban yarda ba, na yi zaton shaƙiyancinta ne kawai". Likitan ya dinga yi musu nasihar 'ya'ya amana ne, don ka aurar da 'yarka ba shi yake nufin ta fita daga hannunka ba har abada, ya zama dole ka dinga bibiya kana sanin halin da take ciki da mijinta, Baba ya yi nadama sosai, jikinsa duk ya yi sanyi, ya fara jin tausayin Sayyada. Likitan ya ce"Idan mijinta ya zo a turo min shi, sannan sai ta farfaɗo za a sake jin ƙarin bayanin cutar da yake yi mata daga bakinta, bai kamata ku bar case ɗin nan, zan iya shige muku gaba ku yi ƙararsa ku ƙwatarwa yarku 'yancinta, domin ya raunata mata zuciya da gangar jiki". Baba ya ce"Anya a yi haka kuwa likita? Lamarin nan aure ne ya haɗa da ba fyaɗe ya tare ta a titi yake yi mata ba, a ganina idan aka kai ƙara kamar an bankaɗa sirrin dake rufe ni, a bar zancen kawai Allah Ya ba ta lafiya, amma dai batun aure babu shi, sai ya sawaƙe mata kawai, idan ya cuce ta Allah zai saka mata". Likitan ya ce"Shikenan, amma duk da haka ku turo min shi idan ya zo, tun da idan ya rabu da ita ai wata zai je ya aura, haka zai yi ta nakasa yaran mutane, yana san ya san hukuncin wannan abin da yake aikatawa da sunan aure, domin fyaɗe ne mummuna, me ya hana ya yi bayanin larurarsa kafin aure?" Baba da Mama suka zauna jiki a mace suna jiran farkawarta, Baba ya kalli Mama ya ce"Amma da ke duk kin ga wannan canjin da ta samu shi ne ba ki faɗa min ba?" Mama haushi ya ƙume ta, ta galla masa harara ta ce"Idan na faɗa maka me za ka yi? Tun da har na faɗa maka hariji ne kuma kai ka san me ake nufi da hariji ai na gama faɗa maka komai, sannan kai ba makaho ba ne, kana kallon yarinyar nan ka san ba ta cikin nutsuwa, amma ka yi biris kawai saboda ba ka sonta, ka ƙi ka yafe mata laifin da ta yi tun a baya, ai ga shi nan yanzu ka kaita inda aka nakasata aka kashe mata rayuwa". Baba ya ce"Wallahi na yafe mata, na daɗe da yafewa Sayyada, kawai dai ni na duba yadda sunanta yake neman ɓaci ne, wannan ya zo neman aure a kore shi wannan ma ya zo, da haka magana za ta dinga yaɗo har wanda bai san ta aikata ba ma ta sani, duka duniya a ji, shi yasa na roƙi Malam Ashiru ya aure ta, saboda na yaba da halayensa, kuma a ganina duk wanda ya ji wannan abin da ta aikata bai ƙyamace ta ba, ai ya cancanci a zauna da shi duk yadda yake, wallahi da na san cutarwar ta kai haka da zaman aurensu bai kai haka ba". Can bayan azhar Mama ta tafi gida ta shiryu kayan da za a buƙata na zaman asibiti, Baba kuma yana zaune ransa duk ya yi baƙi, sai ga Ustaz ya ƙaraso emargencyn, da jallabiyarsa da hirami, ga kuma leda a hannunsa ya siyo lemo na ɗari biyar, ya zo ya sunkuyar da kai ya ce"Baba ina wuni?" Baba ya ƙi kallon shi, bai damu ba ya ce"Ya mai jikin take?" Baba ya ce"Da sauƙi ya ranka?" Ustaz ya ce"Tooo...Baba akwai matsala ne? Na ga kamar ana yi min magana a hasale haka, sannan na lura kamar kana jin haushina, wallahi mukullin na nema na rasa ne, sai da na je na siyo, kuma ina dawowa gidan Allah da ikonsa kawai jiri ya kwashe ni na faɗi ni ma, kuma hakan ya samo asali ne da wato ainahin shi fargaba da na shiga ta wannan laruri da ya samu ita Assayyada, to amma da yake dai hankalina bai gushe ba, sai na tsinci bakina da furta ayoyin Allah, bi ma'ana Allah Ya nufe ni, shi ne a hankali na dawo daidai, yanzu ya jikin nata ta farka? Jinnu ne?" Baba ya ƙi kallonsa, takaici ji yake kamar ya tashi ya shaƙe shi, shi kuma Ustaz bai gane ba, ya yi zaton duk jimamin rashin lafiyar ne ya saka shi banza da shi, ya tashi ya zauna a kusa da Baban, ya cigaba da faɗin"To sai dai wani hanzari ba gudu ba Baba, su fa asibiti idan aka kawo mutum wani lokacin ko sun ga jinya ba tasu ba ce sai sun tsaya sun tatsi kuɗi kafin su faɗawa mutum gaskiya, a gaskiya jinyar Sayyada ba ta asibiti ba ce, akwai shaiɗanun aljanu a tare da ita, waɗanda nake kyautata zaton su ne suka saka mata tsakar auren ma kwata-kwata, sannan idan aka yi duba da yadda take guduna da nuna rauninta a fannin raya sunna, za a iya cewa ƙila aljani jinnul ashiq ne a jikin ta, bi ma'ana ya aure ta, shiyasa ba ya so na dinga raɓarta, ka ga ni kuma ana tauye mini hakkina..." Daidai nan Baba ya miƙe kamar walƙiya, babu zato ya wanke fuskar Ustaz da mari, ya ce"Buhun ubanka kai da hakkin naka!" Ustaz hankali tashe ya ce"Ya subhanallah! Subhanallah, Baba me ya yi zafi haka? Ko dai aljanun nan sun yi magana sun ɓata ni a idonku?" Baba ya sake zabga masa mari ya ce"Uwarka ce mai aljanu, mutumin banza da wofi, ashe cutar yarinya kake yi haka, ka ajiye ta a gida kana so ka haukatata ka kashe ta?" Ustaz ya ruɗe ya ce"Subhanallah! Baba me aka ce ya same ta ne? Amma gaskiya ban tsammaci haka daga gare ku ba, irin yadda na rufa mata asiri na aure ta a yayin da mutane suka guje ta..." Baba ya ce"Koma ka tona mata, na ce bankaɗa asirin kowa ya ji, kuma bari ka ji, ba don na duba rufin asirin da ka yi mata ba da yanzu wata maganar ake yi ba wannan ba, don so aka yi a kai case ɗin ga hukuma, yanzun ma ka je likita yana nemanka, idan ka cuci Sayyada kuma Allah Ya saka mata". Ustaz ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Don Allah Baba a yi haƙuri don Allah, na san na yi kuskure amma in sha Allah zan gyara, kuma wallahi tana da matsalar aljanu a duba lamarin da ai ba haka take ba". A fusace Baba ya nuna masa hanya ya ce"Fice daga asibitin nan tun ban kwantar da kai ba, ka fita na ce kar a yi abun kunya, idan har da sunan duba Sayyada za ka zo asibitin nan kar na sake ganinka, mutumin banza malamin ƙarya, macuci, kuma ka aiko mata da takardarta cikin salama". Ustaz ya ce"To shikenan Baba, yanzu ranka a ɓace yake dai, idan ka huce ma yi magana, Allah Ya sani ban cuci matata na, ni kuma idan an cuce ni na yafe". Duk wannan abin da ake yi bai ajiye ledar hannunsa ba, har ya tafi ya dawo ya ajiye ya ce"Ga wannan tun da na riga na siya, Allah Ya rufa asiri Ya huci zuciya". Ya ajiye ya tafi, bai bi ta kan likitan da aka ce yana neman shi ba ya bar asibitin. Yana tafe gabansa yana faɗuwa, yana karanta La haula wa la ƙuwwata illa billah, babban tashin hankalinsa a yanzu shi ne a ce ya saki Sayyada, samun wacce za ta aure shi ba lallai ya zama matsala ba, amma akwai ƙalubale guda biyu wanda za su iya kawo tsaiko kafin auren, domin ba kowacce mace za ta yarda ta auri talaka irinsa ba, tun da yanzu matan zamanin nan suna da bori da shagala, na biyu kuma yana jin tsoron a yi auren matar ta kasance mai rauni kamar Sayyada, daga lokacin da ya fara auri saki hankalin mutane zai dawo kanshi a fara binciken dalili, idan aka gano shi hariji ne ya zai yi da rayuwarsa? Wannan shi ne abun fargabarsa, don haka ya gama yankewa ba zai saki Sayyada ba duk runtsi, sai dai duk wacce za a yi a yi. Ban farka ba sai dare, ko da na farka ba na cikin hayyacina, cin abinci, wanka, shan magani da allura, wannan duk ina yi ne ba tare da na tuna ko ni wace ce ba, sai bayan kwana uku na dawo daidai, ban yi mamakin ganina a asibiti ba, tun da dama na san a halin da nake ciki komai zai iya faruwa, jikina ya yi min nauyi, amma kaina ya yi sauƙi ciwon kan nan ya ragu da kaso saba'in cikin ɗari, na kalli Mama dake sallaya tana jan carbi, abubuwan da suka faru suka shiga dawo min, na fara hawaye, sai da na fara kuka me shassheƙa sannan Mama ta ankara na tashi, ta zo ta zauna ta kama hannuna ta ce"Sayyada, sannu ya jikin naki?" A hankali na furta Mama me yasa ban mutu ba? Don Allah ki faɗawa Baba ya fahimce ni wallahi ba zan iya wannan zaman ba". Mama ta ce"Shikenan, Babanki ya fahimce ki Sayyada, ki kwantar da hankalinki kin ji?" Na gyaɗa mata kai, amma na kasa jin daɗi da jin wai Baba ya fahimce ni, ta fita ta kira likita suka shigo tare da wani likitan da ban, aka yi min tambayoyin me nake ji, na ce"Ciwon kai kaɗan, zafin zuciya, sannan na gaji da duniyar, na gaji da aure, don Allah a yi min allurar mutuwa idan akwai". Ɗayan likitan wanda ya kasance counselor ya ja kujera ya zauna ya ce"Ki kwantar da hankalinki Sayyada, a nan ba mu da allurar mutuwa, amma za mu iya ba ki shawarwarin da idan kika bi za ki ji ba sai kin mutu ne kika samu maganin matsalarki ba, za ki samu farin ciki ki fita daga ƙuncin da kike ciki, sannan za ki dawo mutum kamar kowa". Na ce"Ba zai yiwu ba, so nake na mutu kawai, ya cuce ni, na tsane shi, ya riga ya kashe min zuciya da gangar jiki mene ne ya rage min kuma? Laifin me na yi ne? Na yi iya yina na gaji, ba ni da wata mafita a yanzu sai ta mutuwa kuma". Ya ce"Tabbas kin yi ƙoƙari Sayyada, kin yi abin da kowa zai yaba miki tun farko ke jaruma ce, daure ki ƙara haƙuri kaɗan, ki ajiye batun mutuwa, a baya kin rasa 'yancinki yanzu lokaci ne na ƙwatar 'yancinki, har yanzu ke mutum ce kamar kowa, kina da damar gyara gobenki, ki manta da batun damuwar mijinki gabɗaya, ki fuskanci sabuwar rayuwa, mijinki shi ya haife ki?" Na girgiza kai alamar a'a ina hawaye. Ya ce"Da shi kika taso tun ƙuruciya ko daga baya kuka haɗu?" Na ce"Sai daga baya". Ya ce"A baya rayuwar da kika yi babu shi mutuwa ce? Kafin haɗuwarki da shi ba ki taɓa yin rayuwa farin ciki ba?" Na ce"Na yi". Ya ce"To kin ga idan haka ne ba shi ne ainahin farincikinki ba, saboda haka mantawa da shi da matsalarsa ba wani babban abu ba ne". Na ce"Ya zama dole na zauna da shi, saboda umarnin mahaifina ne, ba ni da burin da ya wuce Baba ya yafe min, kuma ya ce zamana da shi shi ne tikitin yafiyar". Ya ce"Ai yanzu Baba ya canza, ya yarda ki rabu da shi har abada, kuma ya ce ya yafe miki, kullum yana faɗar ya yafe miki, yanzu ma ya bar asibitin nan, idan ya dawo da daddare za ki ji daga bakinsa". Na yi shiru kawai, sai na ji ban wani ji daɗi sosai ba, na yi zaton idan na ji Baba ya yafe min har daka tsalle murna zan yi, amma yanzu na nemi farinciki na rasa, sannan ba baƙinciki nake yi ba, babu yabo dai babu fallasa, ni dai fatana a ce da gaske zan rabu da auren nan na ƙaddara. Kalaman kwantar da hankali da ƙarfafa gwiwa sosai ake yi mini, a hankali na fara jin nutsuwa, irin wacce na rasa tun ranar da na tare a gidan Ustaz, hankalina ya ƙara kwanciya ganin yadda Baba yake ta nan-nan da ni, yana maimaita ya yafe min, kuma za a raba aurena da Ustaz, abin da ya sa na ƙara yarda shi ne ko sau ɗaya ban ga Ustaz ya zo duba ni ba. Satina ɗaya a asibiti aka sallame ni, sai dai zan dinga ziyartar counselor a sati sau biyu, yana tabbatar da samun lafiyata. Alhamdulillah na ji daɗi da na ga an wuce da ni gidanmu ba gidan Ustaz ba, sannan ga kayan sakawata nan duk an kwaso min, Mama ya cigaba da kwantar min da hankali, na fara warwarewa ina samun sauƙin zuciya sosai, kullum sai Baba ya tambaye ni abin da nake so ya siyo min, kowa tausayina yake ji. Satina ɗaya a gida wataran da yamma Baba yake ce min yau Ustaz zai zo mu tattauna, gabana ya faɗi na ce"Baba me zai yi min?" Ya ce"Ai dole zai zo dama, tun da ba sakinki ya yi ba, a yanzu magana ta ki ce, idan kin ga kin komawa aurensa to da son ranki ne, idan kuwa ba ki amince ba babu wanda zai sake yi miki dole". Hankalina ya ɗan kwanta, amma cikin zuciyata ina fargaba, ko son ganin shi ba na yi. [20/10, 7:45 am] Sadiya Abdulrazak: 24 Haka na yi wunin ranar suƙuƙu kamar mara lafiya, duk da Mama tana ta kwantar min da hankali, ana idar da sallar isha'i sai ga shi ya kira waya, na kalli sunan Malam Ashiru da yake yawo a screen ɗin wayar, gabana ya ba da rass, na ɗauka da sallama, ya ce"Wa Alaikissalam, Assayyaddata". Na yi shiru kamar ban ji shi ba, ya ce "Ga ni a ƙofar gida, ya za a yi? Fitowa za ki yi ko shigowa zan yi?" Sai kawai na kashe wayar, na leƙa tsakar gida kamar zan yi kuka na ce da Mama"Mama wai ya zo". Mama ma gabanta ya faɗi ta ce"To! Anya kuwa ya shigo? Ina tsoron kusancinku da mutumin nan Sayyada". Na ce"Mu tsaya a wajen kawai". Ta ce"A'a ai mijinki ne, babu daɗi ku tsaya a waje, ya shigo ɗin, amma don Allah ki kama kanki Sayyada, ki tuna wahalar da kika sha a hannunsa, da shi kafin ki fara sauraron daɗin bakinsa". Na ce"Haba Mama, sai kace dama son shi nake?" Ta ce"To ai tsakanin mata da miji sai Allah". Na koma ɗaki a raina ina jin lallai Mama ba ta san yadda na tsani Ustaz a raina ba, hijjabi na saka na leƙa ƙofar gidan, da yake layin namu akwai sola, tarr na kalle shi cikin hasken ƙofar gidan, ya sha wata shadda ɗinkin babbar riga kamar wanda zai je ɗaurin aure, ko ma a ce shi ne angon, hannunsa riƙe da wata leda, muka haɗa ido ya washe min baki yana murmushi, na ɓata rai na ce"Ka shigo". Ya biyo ni yana cewa"Assayyada babu ko sallama ballantana gaisuwa?" A tsakar gida ya tsaya ya gaishe da Mama, sannan ya ƙaraso ɗakina, ya zauna idonsa a kaina kamar zai cinye ni don kallo, na ce"Ina wuni". Ya yi murmushi ya ce"Lafiya lau Assayyada, ya jikin naki?" Na ce"Da sauƙi". Ya ce"Ai na ga alama kam, wannan ai kin riga kin warware ma". Na yi shiru. Ya rage murya tare da nakashe ta cikin yaudara ya ce"Assayyadata kin yi ƙiba abunki ma sha Allah ! Ni kuwa ina ta ramewa, shin da gaske ba kya kewata? Ni fa kin ga rashinki ya sa duk na firgice, ko baccin kirki ba na iya yi wallahi, bi ma'ana babu nutsuwar gangar jiki, idan na dawo gidan sai na ga kamar kango, babu mai tarairayata ta ɗauki laurarata, ke fa? Ba kya jin cewa rayuwarki ba ta cika ba saboda ba ma tare? Wai ma don Allah kina sona? Na yi kuskure da ban yi miki wannan tambayar ba, kuma na mayar da hankali don samun amsa, bi ma'ana na fahimci kina sona ko ba kya sona". Na ce"Ɗan Ustaz". Ya yi wata dariya mara sauti sosai ya ce"Sunan da na samu kenan?" Na ce"Bari ka ji na faɗa maka, ni ba na sonka, ban taɓa sonka ba, ai ba ka yi abin da zan so ka ba a duk tsayin zamanmu, don haka ban taɓa kewarka ba, kuma ba na fatan zuwan ranar da zan yi kewar miji irinka". Ustaz ya fara girgiza kai, ya ce"Ya subhanallah! Subhanallah Assayyada ki yi gaggawar faɗin Astagfirullah bi ma'ana ki tuba, saboda kin aikata tsaka-tsakiyan saɓo, e don ba a ce masa babba ba, tun da zai iya yiwuwa suɓutar kalam ne, kuma ni a bisa adalcina na yafe miki, e idan don ta ni ne dai wallahi na yafe, sai dai kuma ya za ki yi da hadisan da suka yi magana a kan girma da hakkin miji a wajen matarsa? Anya kuwa Assayyada?" Na kawar da kai gefe. Ya ce"Kodayake, ni ma da nawa laifin, duba da ganin yadda wato ainafin na biyewa sharrin rauni na zuciya da gangar jiki, na dinga sauke miki buƙatata ba bisa ƙa'ida ba, duk da ba wai na kauce hanya ba ne, Lala-lala ina kan hanya tun da ai hakkina ne, kuma shi harkar raya sunna wanda masu hikima suka ce kashe arna haƙiƙa shi ne auren, idan babu shi babu jin daɗin aure, sannan babu haihuwa, to na sani ban yi duba da ba ki da lafiya ba a ranar da abin ya faru, hakan kuwa ya faru ne biyo bayan kaidi na mace, wato bi ma'ana ke". Hararar da na galla masa ce ta saka shi dakatawa bai shirya ba, ya runtse ido ya ce"Assayyada haƙiƙa da sauranki a sanin darajar miji, ba don ina yafe miki ba da sai kin halaka, kin tashi cikin mata rafkanannu masu yawan zunubi, bi ma'ana waɗanda ba su da rabo". Ya ɗora da faɗin"To abin da ya sa na ce kaidi na mace shi ne wannan farar cinya taki da na gani a daidai lokacin, haƙiƙa ita ce ta ruɗe ni na kasa riƙe kaina, kada ki manta ni hariji ne Assayyada, wallahi a hakan ma ina iya yina don ganin na sassauta miki tun da na gane kina da rauni". Na ce"Tun da har ka faɗa da bakinka kai hariji ne, to Alhamdulillah, idan har kana da adalci ka san ba zai yiwu a zauna zaman aure da hariji da mai lafiya ba ko?" Ya ce"A'a Assayyada ai shi ma hariji ba mara lafiya ba ne, hasalima ya fi kowa lafiya ta wannan fanni, kawai dai halitta ne, da kuma laruri bi ma'ana mu mace ba ta taɓa gamsar da mu ko za mu dawwama a tare, wannan shi ne". Na ce"To ai kamata ya yi a ce ku dinga neman mace harija, wato mai irin lafiyarku, idan kun ga dama kar ma ku dinga tsayawa sallah da cin abinci, tun da dai cewa aka yi abin da aka halicce ku don shi kenan". Ya ce"Subhanallah! Wato mun lura Assayyada kina kaurara harshenki, amma la ba'asa ni dai har zuciyata na yafe miki, sai dai yaya za ki yi da faɗin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama na cewar kada mace ta ɗaga muryarta sama da ta mijinta? Assayyada idan fa ba ki kula ba kin fara yi min biyayya za ki iya shiga halaka al azeem, bi ma'ana halaka mai girma". Na ce"Ba sai na ƙara zama da kai zan halaka ba? Ka ga ka yi maganar da ta kawo ka gidan nan". Ya shiga shafa gemu yana yi min wani fitinannen kallo yana narke idonsa masu cike da sha'awa ya ce"Maganar aure ce Assayyadda, maganar kome, bi ma'ana ta neman sasanci, Assayyada tun da dai Allah Ya sa jikinki ya yi ƙwari, don Allah ki cire komai a ranki, ki wuce mu tafi izuwa gidanmu, domin mu ɗora daga inda muka tsaya, bi ma'ana rayuwar aurenmu ta cigaba, amma fa ba irin ta baya ba". Ya gyara zama ya janyo ledar kusa da shi ya buɗe ta, yana cewa"Idan kika yi duba da abin da yake cikin ledar nan za ki yarda da kalamina na cewar ba irin rayuwar baya ba". Na kalli ledar na ga kaza ce 'yar tsamurmura ta sha gashi, ga ta nan a gudanta ba a yayyanka ba, na kau da kai na ce "A tunaninka saboda ba na cin nama ne zan guje ka". Ya ce"A'a Assayyada, na san ba haka ba ne wallahi, maƙasudin ai batu ne na raya sunna, bi ma'ana kina da rauni a fannin kashe arna, to in sha Allah na yi miki alƙawin za mu yi minus one, kin san a baya ma ai mun yi, ranar da abun ya faru ma wallahi ba don na ga cinyarki ba da ba lallai haka ta faru ba, to wannan kallon ita cinyar ne ya haddasa komai, amma yanzu bisa adalcina na yi miki alƙawarin za a yi minus two, bi ma'ana an cire na rana, an cire na asuba shi ma, sai dai zan dinga dawowa kasuwa kamar ƙarfe shida haka, idan na dawo sai ki ba ni dama ki taimake ni na 'yan mintuna kafin sallar magriba, daga nan kuma sai daren, ai a baya na faɗa miki shi na daren a shi na fi samun nutsuwa". Na ce"Ni fa bari na faɗa maka gaskiya, wallahi na gama aurenka, ba zan sake zama da kai ba, gara ma kawai ka yi wa kanka ƙiyamul laili ka sake ni". Cikin rashin gane magana ta ya ce"Ƙiyamul laili ai ina yi Assayyada, ke ce ma kike da wannan raunin ba kya yi yadda ya kamata, kuma batun saki sai dai na ce Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, subhanallah!". Ya ɗaga hannunsa sama ya buɗe ya fara addu'a ya ce"Ya Allah ni bawanka Ashir ina nemawa matata Assayyada yafiyarka, bisa wannan babban zunubi da ta aikata, wato ma'ana zunubi azeemee, Allah na yafe mata, Allah Ka yafe mata ba don halinta ba, ba don aikinta ba, sai don rahamarka ga bayinka, ya Arhamar Rahimin". Ya shafa a fuskarsa, sannan ya kalle ni a rikice ya ce"Assayyada, shin mantawa kika yi da haramcin mace ta nemi saki babu dalili ko kuwa kin jahilci lamarin ne?" Na ce"E Nei jahila ce kuma ba na fatan na san wa'azin nan na son zuciyarka". Ya yi shiru na ɗan lokaci kafin ya sauke ajiyar zuciya ya ce"Haƙiƙa abun azeemun ne, bi ma'ana mai girma". Ya fara matsowa kusa da ni, yana cewa"Maganar nan ba ta fatar baki ba ce, na lura cewa kin yi kewata, duk da kin fusata, to kuma kin san shi raya sunna irin wannan yana wanke zuciyoyin ma'aurata, bi ma'ana yana kawo sasanci da fahimta juna, daure ki taimake ni ko da al ƙublatu ne, wato bi ma'ana sumba, inda zan yi na minti shida na san za mu iya samun daidaito kafin gobe na zo mu yi zama na musamman". Na matsa gefe ina cewa"Ko zuwa dubu za ka yi ba zan canza maganata ba wallahi, ni da kai zama ya ƙare, ko hannuna ba za ka sake riƙewa ba". Ina rufe baki ya fizgo ni, na faɗa jikinsa, ya rungume ni ƙam, zuciyata ta dinga bugu, na kasa ƙwacewa har sai da ya sassauta riƙon ya fara lalubar jikina sannan na samu damar ture shi, na fita daga ɗakin har ina tuntuɓe, na faɗa ɗakin Mama i a fashewa da kuka, shi kuma ya fice daga gidan ko sallama bai yi wa Mama ba, Mama ta ce"Lafiya? Me ya yi miki?" Na ce"Ba komai". Ta ce"To kukan na mene ne" Na ce"Cewa ya yi ba zai sake ni ba". Ta ce"Shi ne kike wahalar da hawayenki? Saki ai ya zama dole kuwa, don haka ki ma kwantar da hankalinki, ai musulunci bai yarda da zaman aure mai cutarwa a cikinsa ba, shi yasa aka samar da saki, don haka ki rabu da shi, ya ƙaraci zaryarsa har ya gaji ya sallame ki". Na sauke numfashi gabana ya a faduwa, ni tsorona ɗaya kar wataran ya yi min fyaɗe a gidan namu a sha kunya, da alama Mama ba ta gama sanin Ustaz ba ne. Na ɗakko kazar na kai wa Mama, ta taɓe baki ta ce "Ai wannan kazar a baya ne kike buƙatarta ba yanzu ba, wato da nama zai yaudare ki saboda ya mayar da ke kura". Mama dai ba ta ci ba, ni ma kaɗan na ci na ajiye sauran, can wajen sha ɗaya na dare sai ga kiran shi, na ƙi ɗauka, sai da ya yi min kira bakwai a na takwas na ɗauka na ce "Lafiya?" Da irin wannan Muryar da take razana ni, wacce idan na ji na san kwanan zancen ya ce"Assayyadata, me yasa ba za ki taimake ni ba? Ina cike da buƙatar matata da son kasancewa da ke, don Allah ki taimaka, yau ya zan yi? Ai na ce miki za a yi minus two ko? Don Allah ki vedio call mu yi". Na kashe wayar ban ce masa komai ba, na kashe ma gabaɗaya zuciyata na bugu, tunawa da irin rayuwar da na yi, samun nutsuwa ko azaba? Wallahi gani nake kawai ya kashe min sha'awa ko wani auren na yi ba zan sake jin sha'awa da son raya sunna ba, ya azabtar da ni da ni, ya zama kamar horo a wajena ba nishaɗi da nutsuwa ba, na lumshe ido, a fili na ce"Alherin ya kai maka har gadon baccinka Sadam". Hawaye ya zirararo min na share, ina tuna abubuwa masu dama, masu daɗi da akasinsu, haka na kwana zuciyata cike da fargaba, gani nake kamar idan ya matse lamba Baba zai canza shawara ya ce sai na koma. A ɓangaren Ustaz kuwa, a birkice ya koma gida, hankalinsa duk ya tashi, sai da ya yi nadamar taɓa Sayyada, saboda wata fitinanniyar sha'awa ce ta taso masa kamar za ta kashe shi, ya yi wanka wajen sau biyar babu sassauci, ya kwanta ya kasa bacci, ya sauka daga gadon ya dinga zagaye yana sambatu shi kaɗai, kafin dai ya yi tunanin kiran Sayyada ko za ta yarda ta rage masa zafi ko ta waya ne, amma ina, sai ta kasa fahimtar halin da yake ciki, ya dinga juyi a gado, ƙarshe dai sai istimna'i ya yi, wato ya biyawa kansa buƙata da taimakon man shafawar Sayyada wani lotion, yana yi yana Astagfirullah,ya yi wanka wani wahalallen bacci ya ɗauke shi da ƙyar, mai cike da mafarkai barkatar duk a kan kashe arna. [22/10, 7:08 pm] Sadiya Abdulrazak: 25 Washegari da sassafe sai ga kiran shi, ban ɗauka ba, can wajen ƙarfe bakwai ma ya ƙara kira, ban ɗauka ba, sai ji na yi ana sallama da Sayyada, na kalli Mama, ita ma ta kalle ni ta ce"Wane ne kuma da safen nan? Leƙa ki gani". Na saka hijjabi na fita, na ga Ustaz ne tsaye hannunsa riƙe da leda, na haɗe rai ban ce komai ba, shi kuma ya yi murmushi ya ce"Assalamu alaikum, barka da safiya, mu shiga daga zauren ko?" Na juya na koma , ya shiga shi ma, ya tsaya yana kallona yana lashe baki kamar tsohon maye kafin ya ce"Assayyaddata". Ban amsa ba, ya ce"Jiya na kwana da mafarkanki masu birkita mutum da son kasancewa da ke, shi yasa dama na ce zan so na zo na gan ki da safen nan, bi ma'ana na samu sassaucin abin da nake ji a zuciya da gangar jikina, musamman ma dai gangar jikin". Ni dai ina tsaye kamar an dasa ni, ko kallon shi ba na yi, ya ce"Assayyada, don Allah ki yi haƙuri mu koma haka, wallahi sam ba na Cikin nutsuwata, domin sallah ma yau makara na yi, sai ƙarfe shida na yi sallah, kin ga kuwa idan rayuwa ta cigaba da tafiya babu ke haƙiƙa za a samu babban giɓi, bi ma'ana babbar matsala, don Allah mu koma rayuwarmu, ai na faɗa miki na yarda zan canza, zan rage, tun da Hausawa sun ce da babu gara ba daɗi, ko sau ɗaya ne yanzu na yarda, indai dare zai yi na samu inda zan raba a kula da ni a taimake don Allah, ni zan iya dauke miki girki ma da duk hidimarsa gida, domin ki dinga samun hutu don Allah". Ganin ba zan kula shi ba ya ce"Shikenan Assayyadda ga wannan, dama kayan karin kumallo na kawo miki, tun da ai hakkina ne na ciyar da ke ko?" Na ce"Na gode, amma a nan gidanmu ma ba a gaza ba, kuma ba za a gaza ba in sha Allah". Ya ce"Ai dama ni ma ban ce an gaza ba Sayyada, kawai dai sanin hakkina ne shi yasa na ga dacewar na kawo ɗin". Na ce"To an yafe maka". Na juya zan tafi, ya riƙo hijjabina yana kirana murya can ƙasan maƙoshi, na fizge na ce"Don Allah daga yau kar ka sake taɓa ni, idan ba haka ba za ka daina ganina har abada, don na lura ba ka gane karatun da nake yi har yanzu". Ya ce"Subhanallah, Assayyada ni fa mijinki ne, ina da ikon taɓa ki, a yanzu haka ma ina da ikon da zan yi miki umarnin ki shige mu tafi gidana, idan kika bijire kuma ki shiga halaka, ko jiya mawuyacin halin da na shiga kina da zunubi mai girma, kuma sai Allah Ya tambaye ki, amma saboda adalci irin nawa sai na yafe miki, saboda haka ki bi a sannu, ina ta ƙoƙarin mu sasanta kina ta botsarewa, don Allah komai ya wuce Assayyada, za a dinga yin sau ɗaya kamar yadda kike so, zan jure ko da zan cutu". Na ce"Gaskiya daga yau idan ka san ba ka da abin da za ka faɗa min kar ka sake zuwa wajena, don ba zan sake fitowa ba, kai na yaro ba ne da zan yi ta nuna maka gabas kana cewa yamma ce, aurenka na ce na gama shi, ni da komawa baƙin gidanka har abada". Ya ce"Subhanallah, Assayyada..." Na katse shi da faɗin"Kawai ka sake ni ta laluma tun ana ganin sauran mutuncin juna, ba sai an je kotu ba ka kunyata, indai za ka yi wa kanka adalci la san ka cuce ni, kuma zamanmu bai halatta na tun da akwai cutarwa a ciki". Na shige gida, yana ta kirana ban dawo ba, ya gaji da tsayuwarsa ya tafi fa ledarsa. Ina shiga na ga Mama tsaye a tsakar gidan, fuskarta da alamun damuwa ta ce"Ni Sayyada ko dai kina son mijinki ne? Idan komawa za ki yi ki yi bayani ba za a tauye ki ba, sai dai idan ya kashe ki mu ce Allah Ya ji ƙanki". Na ce"Wallahi Mama ba na son shi, ai ke kika ce na fita". Ta ce"Kuma da kike tsayawa kina sauraron shi ba a haka zai dinga kalaman da zai ribace ki ki koma ba? Hmm shikenan, idan za ki koma ɗakinki babu wanda zai hana ki Sayyada". Na shige ɗaki raina har ya fara ɓaci, kuma tun daga ranar na yi alƙawarin Ustaz ba zai ƙara ganina ba, a ranar da daddare da ya zo na ƙi fita, Mama ba ta ce min komai ba, kafin na kwanta bacci ya kira ni ban ɗauka ba, ya dinga jero min saƙonni na roƙo da nuni da yadda yake kewata, tun ina karantawa har na gaji na kashe wayar. Tun daga nan fa kullum sai ya zo amma ba na fita, da ya dame ni da waya na saka shi a blacklist, watarana muna zaune ni da Mama a tsakar gida bayan sallar magriba sai ga sallamar shi, babu neman izini ya faɗo cikin gidan, Mama ta shiga laluben hijjabi, ni kuma na shige ɗakinta da gudu, Mama ta ce masa"Lafiya dai ko?" Ya ce"Lafiya ƙalau, dama Mama a kan maganata ce da Sayyada, ni na san a baya na yi laifi, na yarda ban kyauta ba, na yi abin da zai sa Sayyada ta ƙi ni, amma wallahi yanzu na canza, zan gyara halina, duk yadda ta tsara zaman haka za mu yi, don Allah ki taimake ni Mama ki saka baki, bi ma'ana ta yarda ta dawo mu zauna, darajar mace ɗakin mijinta fa". Mama ta ce"Malam aure na mutum biyu ne, tun da ta ce ba ta yi kawai ka haƙura, ka cutar da yarinyar nan, cutar da idan muka yi ƙararka sai an bi mata hakkinta, amma muka rabu da kai, sannan ba mu hana ka biko ba, muka ba ka dama, sharaɗin dai ɗaya ne ita da kanta ta zaɓa zama da kai ko rabuwa, saboda kar a shiga hakkinta, don haka duk wanda ta zaɓa haka za mu bi". Ya ce"Na fahimta Mama, amma dayake yanzu ta daina fitowa idan na zo, kuma ta daina ɗaga wayata sai ya zamana ba ni da wata hanya da zan iya cigaba da yaƙin bikon, wannan shirun nata yana azabtar da ni, ban san a wani matsayi ta ajiye ni ba". Mama ta ce"To hakan yana nufin ba ta yarda da bikon ba kenan, don haka ka yi wa kanka adalci ka sake ta tun kafin a ɗaga maganar zuwa gaba". Ya ce"Subhanallah! Wallahi ba na jin zan iya jure rabuwa da ita, to idan na sake ta na auri wa?" Mama ta ce"Wannan kuma ya rage naka". Ta tashi ta shiga ɗakin da nake, muka zauna jigum-jigum, ya shiga kirana da murya mai rauni, "Assayyada, Assayyada". Ko kallon ƙofar fita daga ɗakin ban yi ba, haka ya zauna sai da aka yi kiran sallar isha'i ya fita daga gidan, da ya idar ya dawo ya yi zaune a ƙofar gida, sai da Baba ya dawo ya gan shi, ya tashi da sauri ya durƙusa yana gaishe shi, Baba ya ɓata rai kafin ya amsa, ya ce"Malam Ashiru lafiya dai ko?" Ustaz ya ce"A lafiya lau Baba, kuma dama ba domin da matata a gidan ba ba za a dinga ganin yawan zuwana haka ba, Baba da za a tausaya a ba ni ita mu tafi da zuwan nawa zai taƙaita, wallahi zan canza". Baba ya ce"Ita take zaune da kai, kuma na ba ka dama ka yi bikonta, ban tilasta ka sake ta ba, tun da kana ganin ka gama bikon da za ka iya, a yau ba sai gobe ba zan zaunar da ita na ji ra'ayinta na ƙarshe a kan batun aurenku, idan ta ce ta haƙura ku cigaba da zama, ni da kaina zan kira ka ka ɗauke ta ku tafi, kamar yadda idan ta ce ba za ta iya cigaba da zaman nan ba, da kaina zan nema mata takardarta, idan ka ƙi ta laluma zan ɗauki matakin shari'a don ba a kanka aka fara kashe auren hariji ba". Daga haka Baba ya shiga gida, ya bar Ustaz gumi yana keto masa, ya rasa yadda zai yi, da me zai ji? Kullum sai ya sha baƙar wuya kafin ya damu bacci, azumi ma idan ya ɗauka karyewa yake yi, saboda yadda ya sa jarabar son kasancewa da Sayyada a ransa,duk ya firgice kana kallonsa za ka san ba ya cikin nutsuwarsa, ga kwandon zunubi da yake ta kwasa duk dare, saboda ba ya iya bacci sai ya biyawa kansa buƙata, sai dai yana yi yana fatan Allah Ya yafe masa. Da ya koma gida ya kasa zaune ya kasa tsaye, ya fita ya nemi wayar abokinsa ya daka lambar Sayyada, tana shiga ta ɗauka, ya ce"Assalamu alaikum ya Assayyada". Tana jin muryarsa ta kashe wayar, ya dinga kira ta ƙi ɗauka, haka ya haƙura ya koma gida, kwanciya ya yi a kujera yana ta tunanin irin zaman da suka yi da ita, sai yanzu ma ya gane yana sonta ba iya sha'awarta yake ji ba, da ya san haka za ta faru da ya yi haƙuri ya rage yawan buƙatarsa a kanta, da tuni yanzu suna tare, ko sau ɗaya ya samu a kullum ai ya rage zafi, gaskiyar masu iya magana da suka ce maraina kaɗan zai haƙura da babu, shi kam ya ga zahiri, bai ankara ba ya ji hawaye suna sakko masa, a fili ya ce"Ya Allah ga bawanka Ashir, Allah Ya taimake ni ka karkato da zuciyar baiwarka Sayyada gare ni, Allah ba zan iya ba ka iya min da iyawarka, Allah ka yi ikonka a kan lamarin nan, idan kuma zaman ya zo ƙarshe ka ba ni madadinta wacce ta fi ta juriya cikin gaggawa". Dabara ta faɗo masa, ya ɗauki waya ya kunna data, ya nemi lambarta, cikin sa'a ya ga ba ta yi blocking ɗinsa ba, da sauri ya fara yi mata voice, ya ce"Assalamu alaikum, Assayyadata dama so yana zama ƙiyayya? Ban san mace mai neman albarka da gamawa da duniya lafiya tana gudun mijinta har haka ba, ina sonki Sayyada, kuma na ce na gane kuskurena, zan gyara wallahi, idan ma kin ce ba kullum za a dinga lamarin nan ba ni zan jure, bi ma'ana idan an yi yau gobe sai a huta, don Allah ki duba halin da zan shiga, kar ki bari a raba mu, sanyi ne zai shigo, ina azabtuwa ina kuma kwasar zunubi da yawa, don Allah ki gwada ba ni dama, Baba ya ce zai tambaye ki, daure ba don halina ba ki taimake ni ki ce kin yafe min, sannan shi ma ɓangaren cefanen zan gyara, ko busasshen kifi ne za a daure a dinga siya, irin bandar nan ai yana da tsoka sosai, ni dama ɗan abin da nake samu a kasuwar ne babu yawa, sannan kuma ana lallaɓa rayuwa saboda gujewa almubazzaranci da kuma ƙoƙarin zama zuhudu, tun da duniyar ma nawa take? Ki yi haƙuri kin ji, zuciya da gangar jiki na kewarki, daga mai mijinki har abada". Lokacin ina kallace-kallacena a tiktok na ga shigowar saƙon shi, shaf na manta ban yi blocking ɗinsa ta WhatsApp ba, na duba na saurara, muryarsa sai rawa take a voice ɗin, kamar ma kuka yake yi, ko kaɗan ban ji tausayinsa ba, sai ma ƙara tsanarsa da na yi, sakamakon tunawa da irin zaman da muka yi da shi, wanda sai a yanzu ne ma nake ganin ƙoƙarina da wautata da na iya wannan dogon zaman da shi, na danna masa block, ina ajiye wayar dai ga kiran Baba daga tsakar gida, gabana ya faɗi, na tashi na fita na tarar da su zaune tare da Mama, da alama abinci ya gama ci, na zauna a gefe na sunkuyar da kai, saboda jikina ya ba ni maganar Ustaz zai yi min, ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am Baba". Ya ce"Ya kuke ciki da batun mijinki ne? Kun gama magana ko har yanzu ba ku gama samun matsaya ba?" Na ce"Baba mun gama, na faɗa masa ba zan koma ba". Baba ya ce"To ma sha Allah, in sha Allah daga yanzu zan fara iya yi na don ganin an yi abin da ya kamata an wuce wajen, Allah Ya sa hakan shi ya fi alkhairi". Ya ce da Mama"Sai ku saka ranar da za ku je ku kwashe kaya". Mama ta ce"Kuma tun yanzu ba a yi sakin ba?" Baba ya ce"To wannan ƙemararren kina ganin zai yi sakin nan ta ruwan sanyi ne? Ai ƙarshenta sai an kai ga kotu, kuma kwashe kayan shi zai tabbatar masa da cewar an fa gama zama da shi, wannan kamar wani sharar fage ne, da nuni idan yana da hankali". Mama ta ce"To shikenan idan Allah Ya kai mu jibi sai a samu wanda za su je su kwashe". Washegari da safe na ce"Mama ni kam yau ya kamata na je na tattare nawa sauran kayan, ba zan rasa abubuwana masu muhimmanci ba wanda ba na so a taɓa, kin ga gara na je na kwashe nawa". Mama ta ce"Da mukulli a hannunki ne?" Na ce"E akwai su a jakata". Mama ta ce"Amma Sayyada kya je kuwa? Kar fa ku haɗu". Na ce"Mama ba za mu haɗu ba, na san lokacin da yake dawowa daga kasuwa, ina da tabbacin daga ƙarfe tara zuwa kafin azhar ba ya gida". Mama ta ce"Duk da haka dai, ban yarda da zuwanki ke ɗaya ba, ki fara zuwa gidan Anisa ta raka ki". Na ce"To bari na shirya" A zuciyata kuma ban yarda na je neman rakiyar Anisa ba, don ba na yi mata kallon 'yar'uwar da zan yi wani sirri da ita a yanzu. Wajen goma da rabi na shirya na tafi, na samu gidan a rufe kamar yadda na yi zato, na saka mukulli na buɗe na shiga, na saka sakata na buɗe daƙin gadon na shiga na fara duba kayan da zan ɗauka, na gama tsaf, sai na zauna ina kallon ɗakin, da baƙin gadon da aka cutar da ni a kansa, na shiga kitchen na ga alamar yana yin girki, na fito da fulas ɗin shayina, da shi zan tafi saboda kar masu kwasar kaya su fasa min, ina cikin dube-duben na ji ana ƙwanƙwasa gidan, gabana ya faɗi, na je bakin ƙofar ban buɗe ba na ce"Wane ne?" Ustaz ya zaro ido, zuciyarsa ta buga jin muryar abar muradinsa Sayyada, sai ya ji kamar Muryar ce take yi masa gizo, don haka ya sake ƙwanƙwasawa ta sake cewa"Wane ne?" Ya ɗaga hannu sama ya ce"Alhamdulillah, Allah na gode maka, sannan ya yi gyaran murya tare da maƙale ta ya ce"Nisfu hayatynki ne Assayyada". Gabana ya ba da wani sauti rass, rass, nan take nadamar zuwana gidan ta kama ni, me ya dawo da Ustaz gida yanzu? Na shiga tunanin mafita, na buɗe ko kar na buɗe? Wata zuciya ta ce kar na sake na buɗe, na rabu da shi ya gama bugunsa idan ya gaji zai tafi, duk nacinsa ai ba ya wasa da sallah, daga nan zuwa azhar idan aka shiga Masallaci dole zai tafi, wata zuciyar kuwa ta ce na buɗe kawai, idan na ɓata rai babu wata maganar banza da zai iya yi min. Tsautsayi da rabon a yi ya saka ni ɗaukar shawarar nan, don haka na buɗe ina ɓata rai, ya faɗo ciki kamar an hankaɗo shi, yana washe baki ya ce"Alhamdulillah, Assayyada kin dawo, kenan bazata kika yi mini?" Ya danna sakata ya taho gare ni. Na zabga masa harara na ce"Malam ba ni hanya na wuce, kayana na zo ɗiba ai ni da aurenka har abada". Ma juya don tattara kayan, ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yanzu Assayyada dama ba dawowa kika yi ba? Kar ki manta da ba sakinki na yi ba, kin san da haka ko?" Na ce"Na sani, amma dole za ka sake ni ai". Ban yi aure ba na ga mutum ya fara kokawar cire rigarsa, gabana ya faɗi na ce"Me kake nufi ne?" Na ɗauki kayan zan wuce shi, ya damƙo hannuna daidai lokacin da ya zuge tazugensa wandon ya zube a ƙasa, na saki kayan saboda firgici har fulas ɗin shayi ya fashe, na ƙwala ihu ina cewa"Wayyo jama'a ku taimake ni". Muka shiga kokowa, yana son ɗaukata, na ƙi ba shi dama, dukan shi nake ta ko'ina, amma wuya kawai nake sha saboda ƙasusuwan jikinsa, har dai ya yi nasarar kwarfe ƙafata na kusa faɗuwa ta gaba, ya saka hannunsa na faɗa na a kai, ya yi min ɗaukar amarya ya kai ni ɗaki har kan gado, na zabura na miƙe ya mayar da ni, ina zaginsa da kiransa bunsuru, ɗan akuya, ina ihu da neman agajin jama'a amma kamar babu kowa a unguwar nan, tun muna dambe har ƙarfina ya fara ƙarewa, don haka ya samu nasarar kai wa inda yake son kaiwa, bayansa dai ya sha duka, cizon da na dinga gasawa kafaɗarsa bai saka shi ya sare ba, sai da ya yi min abin da ban taɓa tunanin zai sake shiga tsakanina da shi ba, kuma iya son ran shi, har sai da ƙarfina ya ƙare na daina dukansa sai gunjin kuka da nake yi ina yi masa Allah Ya isa, kusan awa ɗaya kafin ya ƙyale ni, na tashi na saka kayana, skert ɗin dai ya yage, a haka na zura hijjabina da yake jalbab ne, na cusa yagaggen a cikin kayan da zan tafi da shi, sai ga shi ya fito daga ɗakin, ko suturta jikinsa bai yi ba, ya durƙusa a gabana yana cewa"Assayyada, ki yi haƙuri don Allah, wallahi ba nufina ba kenan, na kasa saita kaina ne, saboda na tara abun, na yi kewarki, ki dubi Allah ki yi haƙuri ki zauna kawai tun da ban sake ki ba". Ko kallon shi ban yi ba, sai hawaye nake yi, wanda ban damu da sharewa ba, na kwashi kayan na fice daga gidan, yana ta kiran sunana da maƙale murya kamar munafuki. Ina zama a cikin adaidaitasahu na sake rushewa da kuka sosai, gabana wara irin azaba yake yi min, na shiga rayuwar da na yi zaton na barta har abada, a yau na tabbatar da mene ne fyaɗe tsakanin mata da miji, na baya a gidan Sadam duk ƙarya nake yi, na yi nadamar auren Ustaz sau babu adadi, kuma na ji a raina idan duk duniya shi kaɗai ya rage namiji na haƙura da aure har abada. Haka na ƙarasa gida a birkice kamar mahaukaciya, Allah Ya taimake ni Mama tana banɗaki, na yi wuff na shige ɗaki, da ta fito kuma ta yi baƙuwa suka shiga ɗaki, da wannan damar na yi amfani na fito na fara zuba ruwan wanka, Mama ta ce"Waye a nan?" Na ce"Mama ni ce, ina zuwa kwata na faɗa, bari na yi wanka". Kafin ta fito na yi wuff na shige banɗakin, ina jiyo ta a tsakar gidan tana tambayar ban ji ciwo ba? Na ce"E ƙaramar kwata ce". Ina wanka ina kuka, na yi na tsarki na yi na sabulu sannan na fito, na yi ƙoƙari sosai don ganin Mama ba ta gane ba, amma sai da ta zarge ni, saboda yadda idanuna suka yi jawur, da na ce mata kaina ke ciwo sam ba ta yarda, ta rabu da ni ne kawai, na wuni cikin damuwa, na kwana ban runtsa ba, zuciyata sai zafi take yi mini. [23/10, 7:29 pm] Sadiya Abdulrazak: 26 Washegari na tashi da zazzaɓi da ciwon kai, kafin azhar ya rufe ni ruf, na yi rigijib, sai kuka nake yi, ita Mama a zatonta kukan ciwo ne, ba ta san kukan zafin abin da Ustaz ya yi min ba ne, ta ce na je asibiti na ƙi zuwa, na sha magani dai ina ta kwanciya. Aka je kwasar kaya wajen ƙarfe tara, Ustaz yana gida lokacin, suka kwankwasa ya buɗe, suka gaisa a mutunce, suka yi masa bayanin an zo kwasar kaya ne, nan fa ya yi tsalle ya dire ya ce"Kayan wa za a kwashe? Shin kun manta ban saki matata ba ko kuwa magagin bacci kuke yi" Ɗaya daga cikin matan ta ce"Ko ka sake ta ko kar ka saki bai dame mu ba, amma mu dai mun zo mu kwashe kaya, saboda". Ustaz ya ce"A gaskiya ba zai yiwu ba, ko Allah Ya ƙaddara akwai rabuwa a tsakaninmu ba zan yarda a kawashe kaya ba sai ta gama iddarta, don haka ku koma ku faɗa musu kwasar kaya ba yanzu ba, bi ma'ana ban lamunce ba". Ya ja suka ja, ƙarshe dai ya banke ƙofar ya saka sakata, a dole suka juya suka koma, ai kuwa ran Mama ya ɓaci da jin saƙon Ustaz, Baba ya ce a rabu da shi, ni ma raina ya ɓaci, fargaba ta sake kama ni, tsanarsa sai hauhawa take a zuciyata. Ƙarin wani abun takaicin ma sai ga shi ya haɗo kan manyan unguwarsu da na unguwarmu da limamai wai sun zo su yi wa Baba nasiha ya yi haƙuri ya ba wa malam Ashir matar shi, ba a shiga tsakanin ma'aurata, Baba tun yana ɓoye musu dalilin son kashe auren har ya fito ya sanar da su hariji ne shi yasa zaman ba zai yiwu ba, nan Ustaz ya yi farat ya ce ai zai gyara zai rage duk yadda Sayyada ta tsara haka za a yi zaman, wasu cikinsu suka yarda da maganarsa, tare da bawa Baba shawarar a gwada a gani, wasu kuma suka ce rabuwar ce maslaha, domin tabbas ya cutar da Sayyada, ƙarshe dai Baba ya roƙi da su saka shi ya sakar masa 'ya, idan ba haka ba cikin satin nan zai kai shi kotu a san abun yi, haka taro ya watse Ustaz ya ƙi yin saki. Cikin satin kullum sai ya zo, ba na fita, ba dama na kunna data sai na ga voice ɗin shi, ina ga dai aron waya yake yi yana yi min voice, da na gaji na goge whatsApp ɗin duka daga wayar, sati yana cika watarana da daddare Baba ya faɗa min gobe za a je Hizba a fara ta nan, tun a daren ya faɗawa Ustaz ya zo su je Hizba sai a tattauna a ji hukuncin wannan auren nasu, ya ce to zai zo, amma haka aka dinga kiran shi bai zo ba, Baba ya ce mu tafi, muka je Hizba muka shigar da ƙorafinmu, suka karbi lambar shi suka kira, yana ɗagawa suka yi masa bayani tare da ba shi umarnin ya zo, babu jimawa ya zo tare da ƙanin mahaifinsa, sai yanzu na lura da ramar da ya yi, ya ƙara yin zuru-zuru, sam ba shi da nutsuwa, aka sake zube zance aka tambaye shi hakane? Ya yi gyaran murya ya ce"Tabbas haka ne, ni hariji ne, to amma sai dai ban yaudare ta ba, tun farko kafin auren na so na sanar da shi Baba, sai ya ce babu wata damuwa a ɗaura kawai, amma kafin a tare sai da na faɗa mata ita Sayyada ga ta nan, ɓaro-ɓaro ban ɓoye ba na ce mata ni hariji ne, ta ce ita ma mijinta na baya hariji ne, don haka babu damuwa, har ma na ce mata a kullum zan dinga nemanta dau biyar ta ce ta amince kuma har sama da haka ma za ta iya jurewa, sai bayan an tare kuma komai ya canza". Hawaye ya sakko masa ya share, ya ce"Allah ne shaidata, Sayyada ta cutar da ni, tun da aka yi auren nan daidai da rana ɗaya ba ta taɓa barina na ƙoshi ba, tun da kwance take yi min kamar ruwa, ba ta da adalci sam, a ce na ba ta ci, sha, muhalli da sauransu amma ta dinga guduwa saboda 'yar nutsuwar da nake nema daga gare ta? Ga ta nan ai idan sharri na yi mata ta musa". Aka tambaye ni shin ya sanar da ni shi hariji ne? Kunya duk ta kama ni na ce"E ya sanar da ni". Mai yi mata sasancin ya ce"To ya aka yi kika yarda za ki zauna da shi, sannan kuma kika canza magana?" Na ce"Ni ban san abun nashi ya kai haka ba, kuma bayan na gane ba zan iya ba ai na ce masa ya sallame ni amma ya ƙi, zamanmu akwai cutarwa, ya cuce ni, ya saka min jinyar zuciya da ta gangar jiki, ba zan iya cigaba da zama da shi ba, kashe ni zai yi...". Na fashe da kuka Baba ya ɗora da faɗin"Har ciwon damuwa ne ya kamata ta sha jinya saboda wanann larura ta shi, sannan har ciki ta samu ya zube saboda yanayin nashi, Sayyada yarinya ce, ya fi ƙarfinta, ba za ta iya ba, don haka ni ba sasanci na zo nema ba, a raba auren kawai". Ustaz ya ce"Don Allah a yi haƙuri, ni fa na karɓi laifina kuma na ce zan gyara, zan rage za mu daidaita abun, ai na faɗa mata duk yadda ta tsara haka za mu yi". Mai sulhu ya ce"To Baba ka ji, shi sulhu alkhairi ne, za mu so a bar yaran su sasanta, tun da har ya ce zai gyara sai a yi haƙuri a ƙara ba shi dama a gani..." Kukan da ya kwace min ne ya dakatar da sauran maganar da ya kwaso, na ce"Ba na son shi, ba zai iya gyarawa ba, kashe ni zai yi". Shi ma Ustaz ya fara kuka da shassheƙa ya ce"Don Allah ku yi min adalci, kar ku ce na rabu da matata, saboda ina sonta, na san na yi mata abubuwan da za ta tsane ni, amma bi izininllah zan gyara, wannan sabon zama ne za mu fara, ta saba da ni idan ta auri lusari ba za ta ji daɗin zaman ba". Baba ya kafe firr a kan ba za a yi sulhu ba sai dai a raba aure, Ustaz kuma yana ta roƙon a yi haƙuri zai gyara, shi ba zai yi saki ba, suka ba mu kwana uku wai ya yi bikona sai mu dawo, Baba ya faɗa musu ai an daɗe ana bikon abun bai yiwu ba, suka ce mu je dai a sake ba mu dama. Ai kuwa washegari Baba ya saka ni a gaba muka tafi kotu, ya shigar da ƙara, aka kai wa Ustaz takardar sammaci, hankalinsa ya tashi ainun, ya kasa zaune ya kasa tsaye, shi dai ko shaida bai taɓa zuwa kotu ba, a ce yau shi aka kai ƙara? Yanzu fargabarsa ɗaya a yi shari'ar nan wanda ba su san larurar shi ba ma duk su sani, ƙarshe aure ya gagare shi, don haka ya yanke hukuncin ba zai yarda a yi shari'ar nan ba, sai ga shi da daddare ya zo, ya yi sallama da ni na ƙi fita, ya shigo har cikin gidan, Baba dake tsakar gida ya haɗe rai ya ce"Malam lafiya?" Ustaz ya ce"Don Allah ka ba ni dama na yi magana da Sayyada in sha Allah wannan shi ne maganata da ita ta ƙarshe". Baba ya ƙwala min kira, na fito gabana yana faɗuwa, ya ce"Ki je ku yi magana, amma kar ki daɗe". Na ce"To" Muka fita muka tsaya a zaure, yau jikinsa ya yi sanyi sosai, shiru kamar ba zai ce komai ba, sannan ya ce"Assayyada yanzu da gaske rabuwar kika zaɓa? Na faɗa miki zan gyara wallahi". Na ce"Ai kuwa ka faɗa, kuma ka nuna min alamun gyaran a aikace sanda na je gidanka". Ya ce"Wallahi wannan tsautsayi ne, son ki da nake yi ne da kewarki ya hana ni jurewa har na far miki, ga shi na tara abun, amma daga baya na yi nadama, in sha Allah ba zan sake kwatanta irin haka ba, ki gwada ba ni dama ta biyu". Na ce"Ita dama sau ɗaya take zuwa a rayuwa, dama can ba sonka nake yi ba, biyayya na yi wa mahaifina, a yanzu kuwa ko dole mahaifina ya yi min wallahi ba zan koma gidanka ba, na gwammace na shiga duniya". Ya ce"Subhanallah! Allah Ya tsare ki taɓewa Assayyada, tabbas kin nuna min ƙiyayya azeema, amma babu komai ni na yafe miki". Na ce"Ka faɗi abin da ya kawo ka, ni zan koma gida". Ya ce"Hmm ai zan zo daidai wajen, Assayada na yi iya yi na na gane ba kya son cigaba da zama da ni, na yi duk yadda zan yi domin na shawo kanki kin botsare, rayuwar aure ba za ta yiwu dole ba, tun da zai zama tamkar fyaɗe nake yi miki, sannan wannan kwanciya da kike yi min kamar ruwa yana kona min rai, ga shi kuma dama ba kya gyara jikinki, abu ya buɗe kamar ƙofar gari, ga shi salam, kuma ba kya ba ni wata gudunmawa yayin gabatar da ita wannan sunan mai ɗumbin lada, saboda haka..." Ya ɗan dakata ya ce"Saboda haka cikin ladabi da girmamawa, tare da tausayawa halin da za ki shiga na rashina, nake cewa ni Ashir na sake ki saki ɗaya rak, domin kin san shi saki an fi so idan ya zama dole ka yi ɗaya, wannan saki ɗaya ƙila zai zame miki wata dama, saboda ko da kin gaji da zawarcin kin kasa samun wanda zai aure ki, za ki iya yin welcome back, bi ma'ana ki tariyo soyayyarmu mu komawa aurenmu, na gode, kuma ni dai na yafe miki, ina fatan ke ma ki yafe min". Na ji wani sanyi har zuciyata, ana cewa duk macen da aka saki sai ta ji zafi a ranta to ni dai wallahi daɗi na ji, na ce"Na yafe maka, Allah Ya yafe mana bakiɗaya". Ya ce"Alhamdulillah, wannan shi ne saki cikin mutunci, ga takardarki nan, sannan ga wannan dubu biyar ce, sai ki ja jari saboda zawarci babu daɗi". Ya miƙo min, na karɓu iya takardar na ce"Na gode, amma ba na buƙatar jari, ka ƙara akan naka jarin, saboda samunka ya fi na da, ka ga za ka iya daurewa bayan auren ka dinga siyan suga na ɗari biyu kai da matar". Ya ce"To shikenan dai, Allah Ya haɗa kowa da rabonsa, amma a shawarce me zai hana ki bari sai kin gama idda a kwashe kayan? Kar a kwashe kuma ki zo kina kewata, an saba abun nan sau uku ko huɗu kullum, yanzu an zo babu ko sau ɗaya, abun akwai tashin hankali". Na ce"Hankalinka ne zai tashi, ba zan taɓa jin kewarka ba, saboda wahalar abun ka danɗana min ba daɗinsa ba". Ya ce"La ba'asa, ala ayyi hall dai ni duk sanda kika ji kina son komawa ƙofa a buɗe take, sai ki taɓo ni, sai dai wannan damar ta wata uku ce kawai, daga lokacin da kika gama idda damar ki ta ƙare, domin ba zan sake biyan sabon sadaki ba kuma a ba ni ɗumame, na gwammace na zaɓi wata cikin masu so na na aura". Na ce"Ka zaɓa tun yanzu, domin ba zan yi kewarka ba har abada". Ban jira cewarsa ba na shige cikin gidan, na ƙarasa na ajiyewa Baba takardar na shige ɗakina, ina jiyo su shi da Mama suna ta hamdala. Washegari da aka je kwashe kaya bai hana ba, aka kwashe tsaf, muka yi shawara da Baba na ce a siyar da su kawai, ina da kuɗi da Sadam yake ba ni tun ina gidansa, idan an tashi wani auren sai na cika da kuɗin da aka siyar da wannan ɗin na yi wasu kayan, don haka aka siyar, aka saka kuɗin a account ɗina. Wani wasai nake jina, na rabu da alaƙaiƙai auren Ustaz, auren ƙadddara, yanzu me ya rage min? Sai lissafin watannin iddata, abu ɗaya ne ya dame ni shi ne tsohuwar soyayyar Sadam da take taso min ta yi min tsaye a zuciya ta hana ni sukuni, na dinga tuna rayuwar da muka yi kafin aure da kuma bayan aure, a yanzu ko na tuna muguntar da ya yi min ba na jin haushinsa sosai, tun da sai yanzu nake ganin yadda ya nuna nadamarsa ya kuma so mu zauna, amma na bijire a lokacin, a raina na gama yanke idan na gama iddata babu wanda ya fi cancanta na aura sai Sadam, ni da kaina zan nemi soyayyarsa na kuma dage har sai na komawa aurensa a karo na biyu, duk da ina sane da furucin Baba a kan aurenmu da Sadam sai bayan ran shi. Wani lokacin ina yiwa Baba uzuri a kan tsanar Sadam da ya yi, tun da yana tuna yadda ya lalata masa 'yarsa ne, amma ban da abun Baba tun da na yafe ai ya kamata shi ma ya yafe, tun da Hausawa sun ce kowa rai ya yi wa daɗi ba ya mai shi ba. Takarda na samu na rubuta ranar da aka yi sakin, ina ta lissafin daga lokacin da zan yi period na farko, sai dai me? Haka wata ya zo ya wuce ni, ban yi period ba, na ƙara kwana biyar a kai ina jiran zuwan shi amma shiru, abun ya fara ba ni tsoro, da na tuna wannan fyaɗen da Ustaz ya yi min ranar da na je kwasar kaya, na shiga fargabar ko dai na samu ciki? A sace na aika wata yarinya a maƙotanmu ta siyo min tsinken gwajin ciki, ina gwadawa ya nuna positive, sai na rasa me nake ji, farin ciki ko akasin haka? Da gaske nake son haihuwa ina so na ga jinina, amma ya makomar wannan ɗa ko 'yar da zan haifa? Shikenan sai ya taso ba a tsakanin uwa da ubansa ba? Ƙila ma Ustaz ya ce na ba shi ɗan shi, ko kuma na yi aure Sadam ya ce ba zai riƙe ɗan da ba na shi ba, jikina ya yi sanyi, amma ta wani fannin farinciki nake yi a raina. Na kasa shiru a ranar sai da na sanarwa Mama ina da ciki, na yi zaton farin ciki za ta yi, amma sai na ga ta dafe ƙirji ta ce"Ciki? Sayyada kamar ya kina da ciki, ban gane ba, yaushe kika same shi?" Na ce"Mama kafin auren ya mutu mana". Ta ce"A iya sanina duk wannan jinyar da kika yi a asibiti ban ji an ce kina da ciki ba, kuma babu binciken da ba a yi ba a kanka, sannan daga asibiti nan aka wuto da ke, kuma a nan gidan kin yi period Sayyada, ta yaya za ki samu ciki?" Gabana ya fara faɗuwa, na sunkuyar da kai, sai yanzu na ga wautata, shaf na manta da amsa wannan tambayar. Ta daka min tsawa ta ce"Ta ya za ki samu ciki? Na wane ne?" Na fara hawaye na ce"Wallahi Mama fyaɗe ya yi min". Ta ce"Wane ne? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". Na ce"Shi ne, wallahi nashi ne". Mama ta ce"Shi wa?" Na ce"A ranar da na je kwasar kayan nan, har na ce miki na faɗa a kwata, shi ne ya ritsa ni a gidan ya yi min". Mama ta hau salati tana tafe hannu, ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Sayyada me kika yi kenan? Me kika ja wa kanki? To wallahi ban yarda da ke ba, ban yarda kwasar kaya kika je ba, kin je kawai kun haɗa baki da shi, don ubanki kina son shi me yasa kika yi shiru aka kashe miki aure?" Na sake fashewa da kuka na ce"Wallahi Mama ba na son shi, na tsane shi, kawai ƙarfina ya fi, amma ni ban taɓa son shi ba". Mama dai ba ta sake cewa komai ba, har na ƙaraci kukana, ƙarshe ma ta bar min ɗakin. Kunya ta sa na kasa ko motsawa na bar ɗakin, haka za ta shigo ta yi abin da za ta yi ta fita duk ina zaune, sai kiran sallar azhar ne ya sa na fita daga ɗakin, na yi alwala sai na shiga ɗakina na yi sallah, Mama ta biyo ni ɗakin ta kawo min abinci, kaina a ƙasa, ta ajiye tana cewa"Gara ma ki saki jikinki, kin yi yadda kike so ai burinki ya cika, Allah Ya sauke ki lafiya". Haka na dinga zaman ɗaki, ko fitowa taya ta aiki na kasa, har dare da Baba ya dawo, yana ƙwala min kira na ji zuciyata ta tsinke, don na tabbata Mama ta sanar da shi halin da nake ciki, na ji kamar na nitse a ƙasa a neme ni a rasa, haka na fita na shiga ɗakin da suke, kaina a ƙasa na ce"Baba sannu da zuwa". Ya ce"Ke da gaske ciki ne da ke?" Na gyaɗa masa kai alamar e. Ya ce"Kuma kin tabbata na mijinki ne?" Na ce"Wallahi Baba na shi ne". Ya ce"Mene ne dalilinki na munafurtarmu kina gabanmu a cikin gidan nan ki ba shi dama ku keɓe? Kenan neman sasancin da yake zuwa ne har kuka samu wannan damar? Ashe kenan kina son shi mu ne muke yi miki yaƙi a banza ko?" Na ce"A'a wallahi Baba, da na je kwasar kayana ne, ya tarfa ni a gidan". Baba ya kalli Mama da neman ƙarin bayani. Ta ce"E ta ce za ta je ta kwashe abubuwa ta masu muhimmanci a lokacin, sai na ce su tafi da Anisa, a ranar ne dai abun ya faru". Nan Baba ya rufe Mama da faɗan me yasa za ta bar ta ta je ita kaɗai? Mama ta ba shi haƙuri, ya kalle ni ya ce"Yanzu shi mijin naki ya san kina da cikin?" Na girgiza kai alamar a'a. Ya ce"To idan Allah Ya kaimu gobe za ki je asibiti a sake tabbatarwa, daga nan sai na kira shi na sanar da shi, Allah Ya raba lafiya, rabo ne ya riga ya rantse". Na tashi a sanyaye na bar ɗakin, na zauna ina shafa cikina da bai ma fara ɗagowa ba, tun yanzu ƙaunar abin da zan haifa ta shiga raina, sam ba na hango zaman haihuwa da rainon da zan yi a gida. Washegari na shirya na tafi asibiti, niƙabi na saka na rufe fuskata, ina shiga harabar asibitin gabana ya tsinke ya faɗi, sakamakon ganin ƙaddarata, Sadam ne tafe yana amsa waya ya doshi motarsa zai shiga, bai buɗe ba, ya dai jingina a jikinta yana yin wayar, zuciyata ta tsaya cak da aiki, kafin bugun zuciyar ya canza, gabana ya dinga faɗuwa, wata irin ƙauna da kewarsa suka taso min, tsohon tsumin soyayyar shi na shekarun baya ya dawo sabo fil a zuciyata, ya ƙara ƙiba, jikinsa ya goge, duk da baƙi ne kuma ba kyakkyawa ba amma kana kallon fatarsa kana yana cikin kwanciyar hankali, daga inda nake ina jiyo ƙamshin turarensa, ganin bai gane ni ba, ya sa na ɗage niƙabin, ai kuwa muka yi ido huɗu, ya tsaya cak da wayar, kafin na ga ya katse kiran, ya mayar da wayar aljihu, ya tsaya yana kallona, sai na dinga taku ɗaya bayan ɗaya har na ƙarasa inda yake, ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ya ce"Kin gama idda ne?" Na ce"Dama ka san aurena ya mutu?" Ya ce"Ina dai hasashen haka, na san kina gidanku". Na ce"A ina ka sani?" Ya ce"Lokacin da kika yi ciwon damuwar nan, matata tana cikin nurses ɗin da suka kula da ke, a bakinta nake jin labarin". Na ce"Amma ya aka yi ta san ni ce?" Ya ce"Ai tun muna tare da ke na sha nuna mata hotonki, sannan ta san sunanki ma". Na ce"Ta haihu ko?" Ya ce"Ki je gida za mu yi waya anjima, Please ki ɗauka idan na kira". Na ce"To". Ya shiga mota ya ja, na shiga asibitin ina waiwayen shi kamar wata doluwa. [25/10, 9:37 pm] Sadiya Abdulrazak: 27 A raina kuwa mamaki nake yi ashe matar shi ta san ni, har ma tana kai masa rahotona? Ni kuwa ban santa ba, kuma zan so na santa, ana yi min gwajin jini aka tabbatar da ina da ciki, na san na wata ɗaya ne, don haka ban yi wahalar yin scanning ba, na koma gida zuciyata cike da kewar Sadam da son kafa sabuwar rayuwa da shi, a yadda na ga soyayyata da tausayi a idonsa na tabbata zai iya aurena, to amma zai iya jirana har na haihu? Kuma ina makomar yaron da zan haifa? Zan rabu da shi ne idan ya ce ba zai riƙe ni da ɗana ba, ko kuwa ma uban ɗan zai karɓe abunsa? Da wannan tunanin na koma gida, kaina har ya fara ciwo, Ustaz ya shammace ni, amma ta wani fannin ya taimake ni, tun da ya ba ni abin da nake nema, wato haihuwa. Ina shiga gida Mama ta tambaye ni cikin ne? Na ce"Mama shi ne". Ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Mamaki ya kama ni, na fara tunanin shin Mama ba ta so na haihu ne a rayuwata da ta tada hankalinta don na samu ciki ko kuwa? Na ce"Mama wai me yasa kika damu?" Ta ce"Ke ba ki damu ba ko?" Na ce"E". Ta ce"Sayyada na san kin ɗauki lokaci ba ki haihu ba, ga ƙannenki nan duk da yaransu, dole za ki so ki haihu, amma ban so kika samu ciki a wannan gaɓar ba, akwai yiyuwar mijinki ya mayar da ke, sannan idan ma haka ba ta faru ba to fa za ki yi doguwar idda, sai kin haihu kin yaye ɗan kafin ki yi wani auren, ban so ki yi wannan da ƙuruciyarki ba". Na ce"Mama ko zan dawwama ban yi wani auren ba, indai na haihu to na gode Allah, kuma zancen kome babu shi har abada". Ta ce"To shikenan, Allah Ya rufa asiri, Ya sauke ki lafiya". Na shiga ɗaki na kwanta ina ta tunani da shafa cikina, na ji ƙarar shigowar saƙo wayata, na duba na ga daga Sadam yake, cewa ya yi na kira shi idan na koma gida, na saka wayar a silent don kar ya kira a ji ƙara, sannan na kira shi, bai ɗauka ba, da ta katse ya kira ni, na ɗauka zuciyata na bugu, ya yi sallama, na amsa wata tsohuwar soyayya na hayewa can saman zuciyata, Allah Ya sani ina son Sadam, ban san me ya hau kaina ba a wancen lokacin har na zama kamar babbar maƙiyiyarsa. Ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ya ce"Ya kike ya bayan rabuwa?" Na ce"Bayan rabuwa babu daɗi". Ya ce"To mene ne ya faru?" Na yi shiru. Ya ce"Faɗa min kin ji, me ya faru da ke mara daɗi bayan rabuwarmu?" Sai na fara siririn kuka na ce"Komai ma". Ya ce"Me ta yi miki zafi haka har kika kamu da depression?" Na ce"Ai tun da na rabu da kai rayuwata ba ta ƙara daɗi ba, ban san ina sonka ba sai da muka rabu, don Allah ka yafe min". Ya ce"Na yafe miki Sayyada, ai ban ƙullace ki ba ni, na yi miki uzuri, sai dai abu ɗaya za ki yi min yanzu na daina tuna abin da kika yi min, shi ne ki aure ni duk runtsi, yaushe za ki gama idda?" Na ce"Ba yanzu ba". Ya ce"Kamar ya?" Na ce"E, ai ina da ciki kuma wata ɗaya ne". Sadam da sauri ya ce"Ciki!? Da gaske kina da ciki Sayyada?" Na ce"Ina da ciki, abin da ya kai ni asibiti kenan, kuma an tabbatar min, wata ɗaya ne". Ya ce"Subhanah! Kenan dai yanzu aurenmu ba mai yiwuwa ba ne ko?" Na ce"Me yasa ba zai yiwu ba? Ba za ka iya jira na haihu ba?" Ya ce"Ki yi haƙuri Sayyada, ai ba ma iya jiran ba ne matsala, gaskiya muddin kika haihu da wani ba ni ba to na haƙura da ke har abada, ba zan iya aurenki ya zama kina samun wani link ɗin da zai iya sada ki da tsohon mijinki ba, tun da ko ɗan kika kalla za ki iya tunawa da mahaifinsa". Gabana ya shiga faɗuwa na ce"A'a Sadam, a'a don Allah, mu ɗauki wannan cikin a matsayin ƙaddara, Allah Ya yi ba kai zan fara haifawa ɗan fari ba, amma indai har yanzu kana sona wannan ba zai hana aurenmu ba". Ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am" Ya ce"Zaman cikin nan a jikinki daidai yake da rabuwarmu, wallahi indai kika ce sai kin haife shi zan iya yafe duk wata soyayya da nake yi miki, idan har kina sona ya zama dole ki zubar da cikin nan". Na ce"A'a don Allah kar ka yi min haka, ina son na ga jinina, kowa ya haihu sai ni kaɗai, ba zan iya zubar da cikin nan ba wallahi". Ya ce"To shikenan, ki zauna da cikinki, amma ki manta da ni da soyayyata, kar ki sake mafarkin za mu yi rayuwa a nan gaba, ke kaɗai ce ba ki haihu ba? Yanzu idan kika yi haƙuri kika zubar da wannan ɗin ba aurenki zan yi ba? Kuma na ce ki dake planing ne? Haihuwa za ki yi, kuma zan iya sakin matata ma don mu fi samun farinciki, indai za ki riƙe min 'yata". Na ce"Au kai ma matarka ta haihu?" Ya ce"E, 'yar watanta uku". Na ce"Ka ga kai kana da madafa, ni ma don Allah ka yi min adalci ka bar ni na haihu". Ya ce"Sayyada, na hana ki haihuwa ne?" Na ce"A'a, amma ai ka jingina sharaɗi a jikin haihuwar tawa". Ya ce"Amma dai ban ce dole ba ko?" Na ce"Kusan dole ne, tun da ba na jin zan iya jure rashinka". Ya ce"To sai ki zaɓa, ko ki zubar da cikin ko kuma mu rabu kawai". Kamar zan yi kuka na ce"Amma..." Ya kaste ni da faɗin"Ba wani amma, Malama ko ki zubar ko ku rabu, duk abin da kika yanke sai ki kira ni, don Allah idan ba ki gama shawara ba kar ki sake ki neme ni, raina zafi yake min, wai Sayyada ke ce kika sakarwa wani jiki har ya ɗirka miki ciki ko? Hmm". Ya katse wayar, na ajiye wayata ina mamakin shi, sai ka ce shi ba wata macen ya ɗirkawa cikin ba, sai nawa ne zai yi zafi? Ko kuma gani yake ba na kishinsa ni? Idan kishi ne ai ni ya kamata na fara, tun da dai ya riga ni yin auren. Nan kuma na shiga tunanin maganarsa, ina son Sadam sosai, shi kaɗai nake son aura, amma kuma shi ma cikin ina son shi, ina so na ga jinina, na kamu da son abin da yake cikina, na shiga tunanin wanne zan zaɓa? Shin yaushe Sadam zai fara yi min adalci? Ta ya shi ya haihu ni zai hana ni? Jikina duk ya yi sanyi ƙalau, ga shi kamar riɓanya min soyayyar tashi ake yi. SADAM Shi kansa ya san ya saki Sayyada ne kawai saboda an kai matakin da dole sai ya sake ta ko ba ya tsoron Allah, tun da yana son rayuwarsa, amma daga baya tausayinta ma yake ji, kuma yana jin sonta ko kaɗan bai ragu ba a zuciyarta, silar wannan abun da ya faru sai da ya yi wa matarsa saki ɗaya, saboda ta tisa shi a gaba da zagin Sayyada da aibata ta, ya rasa da wanne zai ji, tsakanin zafin ciwon jikinsa da na zuciyarsa wato rabuwa da Sayyada, ga kuma magana a wajen Safna ta ƙi ƙarewa, ya yi mata gargadi ba ɗaya ba, ba biyu ba, ƙarshe ya ce idan ta sake zagin Sayyada a bakin aurenta, tsautsayi ya sa ta sake ai kuwa nan take ya sake ta, Momy har mari ta zazzabga masa, ta ce maza ya je ya mayar da matarsa, shi ne ya mayar da ita, sai bayan ya rabu da Sayyada ne ma yake ƙara jin sabuwar soyayyarta a zuciyarsa, ya dinga kewarta, ya fi samun cikakkiyar gamsuwa idan da Sayyada ya raya sunna, ko fa kuwa fyaɗen da ta ce yana yi mata ne, ya fi masa daɗi a kan kasancewa da Safna, wata irin raguwa ce mai rakin tsiya, minti goma ma sai ta ce ta gaji, ta yi ta mita, shi kuma ƙa'idarsa minti talatin ne zuwa sama, haka ta dinga gudunsa, wataran ma ya san ƙalau take amma sai ta yi masa ƙaryar ba ta da tsarki, wannan ma ya sa shi kasa mantawa da Sayyada. Lokacin da ya ji Sayyada ta fara soyayya da wani, ba ƙaramin tashin hankali ya shiga ba, domin shi a zatonsa son da take yi masa ba zai barta ta iya auren wani ba, za ta gwammace ƙarasa rayuwarta a haka, tun daga lokacin yake bibiyar lamarinta, shi ya je ya samu wanda zai aure ta ɗin ya sanar da shi sirrikanta da ba kowa ya sani ba, ya ɗaura ɗamarar sanarwa da kowa, shi bai ƙi a ce duk duniya ta sani ba, fatansa da ribarsa ɗaya ne, kawai kowa ya guji Sayyada, a bar masa ita idan ta yi kwantai kafin lokacin da zai waiwaye ta don su dawo da rayuwarsu kowa ya haƙura, kuma a lokacin zuciyar Iyayensa ta yi sanyin da za iya haƙuri su amince da ita a karo na biyu, a auren da za ta yi ya tura mace ta faɗawa wanda zai aure ta ne ga abin da ta yi amma ya nuna zai aure ta a haka, shi yasa ya ɗauki wata ya biya ta, ta ke ta sanarwa da Mahaifiyarsa aka yi nasarar fasa auren, shi Ustaz ne dai bai san komai ba sai auren ya ji kawai, amma da ya tsananta bincike ya ji hariji ne sai ya hankalinsa ya kwanta, domin a zatonsa ba za ta iya ko sati ɗaya da shi ba, amma sai ya ji shiru ta yi zamanta, lokacin da ta yi ɓarinciki Safna ta fara haɗuwa da ita a asibiti, ta faɗawa Sadam ɗin ta ga tsohuwar matarsa a asibiti ta yi ɓarin ciki, kamar ya yi wa Sayyadar magana ya yi mata sannu sai ya bar shi, sannan shi ya tura mata kuɗin 'yan haya da ya saka a gidan, ya ɓoye mata ne saboda kar ta san shi ne ta ƙi karɓa, kuma a ranar da aka kawo ta asibiti ba ta cikin hayyacinta Safna ta faɗa masa, to a lokacin har faɗa suka yi da ita, saboda yadda ya nuna damuwarsa a kan halin da Sayyadar ta shiga, tun daga nan ya yanke ta daina faɗa masa wani abu da ya danganci Sayyada, ita dama tana faɗa ne don ya gane Sayyadar fa ta manta da shi, tana can tana rayuwa da mijinta, to da ta ji wannan matsalar ta faru kuma ana raɗe-raɗin wannan sai dai ma auren ya mutu shi ne Safna ta daina faɗawa Sadam, shi kuma kullum sai ya tambaye ta ya jikin Sayyada, ta ji sauki? Sai a lokacin ta fara kishi da ita. Shi dai a yanzu a shirye yake ya yi fito na fito da kowa saboda Sayyada ta dawo ƙarƙashin kulawarsa, amma dole sai ta cire cikin jikinta, duk da barazana kawai yake yi mata, ko ta ƙi cire cikin dole zai haƙura ta haihu ya aure ta, amma zai gwada matse lamba ya gani idan ba ta cire ba shi Kenan. USTAZ ASHIR Tun da ya saki Sayyada yake yin wata irin rayuwa mai wahalar gaske, sai yanzu yake jin son Sayyadar ma, ga kuma azababbiyar sha'awarta, tsofaffin kayansa na ɗakinsa kafin ya yi aure su ya ɗakko yake yin shimfiɗa yana kwana a gidan, da safe sai ya koma gidan iyayensa ya ci abinci, da daddare ya yi ta fama kafin ya samu bacci, yana biyawa kansa buƙata yana istigfari, ya haƙura da Sayyada, ya matsu ya yi wani auren, amma yana fargaba kar a kuma irin na Sayyadar, a yi masa ta leƙo ta koma, a ɗanɗana masa zuma a baki a janye, shi yasa yake kama kansa. Akwai wata yarinya da ta taɓa cewa tana son shi, ranar sun je sun yi wa'azi a wata walimar aure da aka yi a gidan su yarinyar, ta auren yayarta, shi ne ta karɓi lambarsa, suna gaisawa, har dai ta nuna tana son shi, shi ne yake ta hanya-hanya saboda 'yar masu kuɗi ce yana ganin kamar ba shi da halin da zai iya riƙe ta, har yanzu dai suna waya jifa-jifa, tun kafin ya auri Sayyada suke tare, yanzu sai ya ga me zai hana ya gwada sa'arsa? Don haka bayan rabuwarsu da Sayyada ya fara ƙarfafa firar tasu, har ma ya saka ranar da zai je, sai dai a wannan karon ya yanke duk wacce zai aura sai ya faɗa mata larurarsa, idan ba ta amince ba shikenan, Idan kuwa ta amince wallahi ba zai sake ta ba, sai ya more sadakinsa har da alakoro. Ana cikin haka sai ga Baban Sayyada ya kira shi ya ce ya zo yana neman shi, ya cika da mamaki, gefen zuciyarsa kuwa farinciki yake yi yana fatan Allah Ya sa dai Assayyada ce ta fara kewarsa ta nemi a yi kome, har wanka ya sake yi, ya saka kaya masu kyau na ƙasan akwati, ya fesa turare ya kama hanya bayan sallar isha'i. Baba ya yi masa iso har cikin tsakar gida, ina ɗaki ya ƙwala min kira bayan isowar Ustaz, na fito, ina kallon shi gabana ya faɗi, raina ya ɓaci, don dole na zauna na gaishe shi, na mayar da kaina ƙasa, suka gaisa da Baba, Ustaz ya ce"Ma sha Allah! Baba lya kira ni, Allah Ya sa dai kiran alkhairi ne". Baba ya ce"Alkhairi ne in sha Allah!". Ustaz ya fara hango tabbatar hasashensa, ya ce"To Alhamdulillah, ma sha Allah". Baba ya ce"Malam Ashiru idan ba ka manta ba akwai ranar da Sayyada ta je ɗiban kayanta a gidanka kafin auren nan ya mutu hakane?" Ustaz ya ce"A ƙwarai hakane, don wannan rana ba zan manta da ita ba". Baba ya ce"Shin wani abu ya shiga tsakaninku a ranar?" Ustaz ya ce"Ƙwarai kuwa, haƙiƙa ta na ni haƙƙina a wannan ranar Alhamdulillah!". Baba ya ce"Ma sha Allah! Allah mai yadda Ya so, to malam Ashiru a wannan haɗuwa taku Allah Ya yi ikonsa, rabo ya shiga tsakaninku, a yanzu haka Sayyada tana da cikin wata ɗaya, an samu tabbaci daga asibiti". Ustaz ya washe baki ya she"Allahu akhbar, Alhamdulillah, ma sha Allah! Allah mun gode maka". Ya kalle ni ya ce"Assayyada kin ga ikon Allah ko? Kin ga ashe rabo ne ya kawo ki gidan a wannan sa'in ko? To Alhamdulillah yanzu ya ake ciki? Amm Baba ko za ka ɗan ba mu waje?" Baba ya tashi ya shiga ɗaki, shi kuma ya matso kusa da ni, na yi saurin matsawa, ya ce"Assayyada ashe ke ce za ki kawo min jinina duniya? Alhamdulillah! Yanzu ya kenan?" Na ɓata rai na ce"Na me kenan?" Ya ce"Wai da na ga an samu rabo, sai nake tunanin ko za ki haƙura ki yafe min, sai ki dawo gare ni, bi ma'ana a yi kome, amma fa ba dole sai kina so". Na ce"Ba na so, kuma ba zan so ba har abada". Ya ce"To a gaskiya Assayyada ni ba zan yi miki dole ba, kar na je ki mace min a gida, to sai dai ga ki sani tun da kina da ɗana ko 'yata a cikinki haƙiƙa ba a rabu ba, bi ma'ana zan dinga zuwa kullum ina ganin lafiyar ɗana, idan ta kama ma za ki buɗe min cikin na ga yanayin kwanciyar, sannan kuma na kai hannu na shafa shi, tun da babu damar kai masa ita babbar ziyarar, bi ma'ana idan an je yaƙi an gama kashe arna shi ma na ciki akan kai masa ziyara ai, to yanzu a madadin haka, za ki buɗe min cikin ina shafawa, domin ya taso da jin ƙauna ta uba a zuciyarsa ba wai iya ɗuminki zai sani ba, sannan kuma bayan Allah Ya sauke ki lafiya kin yaye shi, zan keɓi ɗana, bi ma'ana ba zan bari ya taso a matsayin agola ba, ko kuma goyon kaka, duk macen da na samu ta yi mini adalci ta iya zama da ni da larurata, wannan ɗana ko 'ya rabonta ne, ina fatan dai la ba'asa ko?" Na ce"Ciki dai ga shi an sanar maka ka san da shi, tun da fatar cikina za ka gani idan ka kalli cikin ba shi ba to wallahi ba zai yiwu na dinga buɗe maka ciki ba kai ba likita ba, zuwan naka ma ba shi da wani amfani, tun da idan na yi magana ba jin muryarsa za ka yi a cikin tawa ba, ba na ƙaunar ganinka, don Allah ka siyawa kanka mutunci kuma ka riƙe shi tun ban tattaka shi ba, idan na haihu na yaye sai a yi duk wacce za a yi". Ya ce"To la ba'asa, shikenan Assayyada, na yafe miki, e wallahi idan don ta ni ne Ni ba baƙon zafi ba ne, na yafe miki, sai dai kuma ya za ki yi da hakkin raba uba da ɗa da kike ƙoƙarin ɗauka?" Na tashi a fusace na ce"Na raba ɗin, wa'azin ƙarya kawai na son zuciya". Na shige ɗaki na bar shi yana ta rafka salati kamar an yi masa mutuwa, ya leƙo ɗakin nawa ya ce"Shikenan Assayyadda, na gode sosai, sannu kin ji, sannu da dakon ciki, ina tausaya miki, ina fatan Allah Ya sauƙaƙa miki laulayi, sannan kullum zan dinga zuwa, kuma zan dinga taho miki da saƙo, bi ma'ana kayan ƙarin jini ingantattu". Na yi banza da shi, ya ce"Assayada". Na juyo na kalle shi. Ya rage murya ya ce"Zan kwana da kewarki". Na yi tsaki, ya wuce ya tafi. 08028966015 [26/10, 7:55 pm] Sadiya Abdulrazak: 28 Kafin na yi bacci sai da na kira Sadam, bai ɗauka ba, ban fasa kira ba, sai da na ga shigowar saƙon shi, ya rubuto min"Ina kusa da matata, kamar yadda yau kika gayyato tsohon mijinki gidanku, ya mayar da ke ko ba ku gama sasantawa ba?" Duk sai na ruɗe, na tashi zaune, fargabar zargin da yake yi min ta danne kishin ce min da ya yi yana kusa da matarsa, na yi masa replay da faɗin"Wallahi ba abin da kake zato ba ne, Baba ne ya kira shi ya sanar da shi ina da ciki, bayan haka babu wata magana a tsakanina da shi, tun da ɗansa ne ka ga dole a faɗa masa ya san da cikin". Ina ta jiran amsar shi shiru, raina duk ya ɓaci, na fara tunanin yana can maƙale da matarsa, haka na yi bacci cikin zulumi da ɓacin rai. Washegari da safe wajen ƙarfe takwas sai ga kiran shi, na ɗauka muka gaisa sama-sama ya ce"Me kike cewa jiya? Kika ce wai an sanar da shi zaman cikin ne?" Na ce"E". Ya ce"To kuma cikin da za a zubar mene ne ma amfanin a dinga wani tereren shi?" Na ce"Ba terere ba ne, shi ai dole ya sani". Ya ce"Da wannan damar zai yi amfani ai ya mayar da aurenku ko?" Na ce"A'a fa, babu batun kome". Ya ce"Dole za a yi shi nan gaba, ni hankalina ba zai taɓa kwanciya ba sai na ga kin gama iddarki, kuma tun da ga hanya mafi sauƙi da za ki gama idda me zai hana a bi kawai? Cikin nan fa yana fita kin gama idda, sai mu fara sanin inda muka dosa". Na ce"Ni fa ina jin tsoron zubar da cikin ne, ɓari yana da ciwo, na yi har sau biyu, sannan na san yawan yin shi matsala ne, ina fargabar abin da zai biyo baya wallahi, kuma ina son haihuwa sosai". Ya yi tsaki ya ce"Kawai ki ce kina son mijinki dai, kina so ki koma gidansa ki haihu a can, wannan shi ne". Na ce"Wallahi ba haka ba ne". Ya ce"Kin ga Sayyada ni ba yaro ba ne da za ki raina min hankali, ki je kawai ki haihu ki koma gidan mijinki Allah Ya raya Ya ba ku zaman lafiya". Kafin na yi magana ya kashe wayar, na dinga kira ya ƙi ɗauka, haka na haƙura, na yi wunin ranar suƙuƙu da ni, ana sallame sallar Isha'i sai ga Ustaz yana sallama da ni, baƙinciki ya ƙara ƙume ni, Allah Ya taimake ni Baba yana nan, ya ce kar na fita bari ya ke ya ji da me ya zo. Ustaz yana tsaye da ledarsa a hannu, ya duƙa ya gaida Baba, Baba ya amsa yana haɗe fuska ya ce"Malam Ashiru lafiya dai ko?" Ustaz ya washe baki ya ce"Lafiya ƙalau Baba, dama na zo duba lafiyar ɗana ne". Baba ya ce"Kamar ya? Dama kana da wani ɗa a cikin gidan nan ne ko dai ɓatan hanya ka yi?" Ya ce"Baba ɗaba da ke tare da Sayyada nake nufi fa". Baba ya ce"Ka zo ganin ɗan ko uwar ɗan?" Ustaz ya ce"To la ba'asa idan ma dukansu ne zan gansu". Baba ya haɗe rai ya ce"Kai Malam Ashiru, tsaya ka saurare ni da kyau, ka fita idona na rufe, daga yau kar ka sake ƙafarka ta sake tako gidan nan da sunan zuwa wajen Sayyada, ba zai yiwu ba, kai ban da zuciyar musulunci ma ta sa mun yi maka afuwa har ka isa ka dinga sintirin zuwa gidana? To ka kiyaye ni, ɗan a hannunta yake ballantana ka ce ƙarba za ka yi? Kar na sake ganin ƙafarka a gidan nan daga yau, idan ta kama a neme ka zan kira ka, babu wata kulawa da za ka ba ta wacce za ta gagare mu". Ustaz ya ce"To shikenan Baba, amma ni ma da na duba na ga har yanzu Sayyada a cikin iddata take, a ƙa'ida ma ni ne zan dinga ciyar da ita, to amma ganin ba za ku bari ba yasa ban yi wannan yunƙurin ba, sai kuma na ce to duk da haka ya kamata na yi wani huɓɓasa, bi ma'ana na dinga kawo mata abubuwan ƙarin jini kullum, kamar zogale hala da 'yar kankana tun da yanzu lokacinta ne, amma ya kake gani?" Baba ya ce"Mun gode, ba ma buƙatar komai daga gare ka, idan aka zo kan gaɓar da kai ne dole ka yi za a neme ka". Ustaz ya yi shiru yana jimami shi kam ya so a bar shi ya dinga ganin Sayyada kullum, ya ce"Shikenan Baba, haka ma la ba'asa, ga wannan tun da yau na riga na siyo". Ya miƙa masa ledar, Baba ya karɓa ya ce"Allah Ya amfana". Ya shiga gida ya bar Ustaz yana shafa gemu. Ina zaune Baba ya miƙo min leda, ya ce"Ga wannan inji mijinki, Sayyada idan kin san ba so kike ki koma gidansa ba to kar ya zo ki dinga fita barkatai, ko waya ban ga amfanin ku dinga yi ba". Na ce"To". Na buɗe ledar, zogalen ya ba ni sha'awa, na hau ci kuwa, sai da na kusa cinyewa na tuna ban yi wa Mama tayi ba, na tura mata ledar na ce"Mama ga zogale". Ta ce"A'a ki ce ke kaɗai, ke ce kike yunwa". Na ce"Mama yunwa kuma?" Ta ce"To idan ba yunwa ba daga kawo zogalen ba tunanin komai ki tusa shi a gaba? Haka kazar nan da ya kawo kika ci son ranki, ko tsoro ba kya ji, yanzu idan ma wata mallakar yake sakawa a ciki shikenan sai a wayi gari kina son shi da son komawa gidan shi". Mama tana rufe baki tari ya sarƙe ni, sakamakon ƙwarewa da na yi da zogalen bakina, tsoro ne ya kama ni, na naɗe sauran zogalen na kai cikin shara, na kuskure bakina, na dawo na zauna jikina ya yi sanyi na ce"Yi haƙuri Mama, daɗi ya min ne". Ta ce"Haƙuri ke ya kama Sayyada, idan zogalen kike so me yasa ba za ki faɗa ba a dinga dafa miki?" Na yi shiru, na tashi na koma ɗaki na zauna na fara gwada layin Sadam, haka ta dinga ringing bai ɗauka ba, na gaji na haƙura, wasa-wasa sai da ya yi sati ba ya ɗaukar wayata, na yi masa massage babu amsa, a cikin sati na biyun ne na samu ya ɗauka, muka gaisa sama-sama na ce"Me na yi maka don Allah?" Ya ce"Ba ki yi min komai ba, amma idan kin san ba wai kin yarda da batun zubar da cikin nan ba ne kar ki sake kirana daga yau, domin ban ga amfanin alaƙar ba". Na ce"Ina son haihuwa wallahi". Ya ce"Zai fi kyau ki ce kina son mijinki, ki ma daina fakewa da yaro". Na ce"Wallahi ba haka ba ne". Ya yi tsaki ya ce"Ina da abun yi". Na sake kira bai ɗauka ba, duk na damu, ƙarshe ma sai ya saka ni a blacklist, hakan ya tabbatar min da gaske yake, na daina walwala ga yawan ciwon kai, sai dai na zauna a ɗaki na yi ta tunani, na rasa me yasa mutane suke da son kansu, ina son haihuwa sosai, amma ina son Sadam, ina fargabar ya ƙi aurena, na firgita da auren Ustaz, na tsorata da maza, ina fargabar idan ban auri Sadam da na saba da shi na san halinsa ba wa zan aura? Kar na auri wanda ya fi Ustaz tsanani, shi yasa rafkananniyar zuciyata ta fara raya min ko na amince kawai, tun da idan ya aure ni komai zai wuce na fara haihuwa, na yi masa massage na ce don Allah ya ɗauki wayata na gaji da yadda yake azabtar da ni, bayan awa ɗaya ya kira ni, ya ce"Sayyada ke ce kike azabtar da mu, na tabbata na fi ki shiga damuwa da tashin hankali, yanzu a ce ina kallo ina ji ina gani wani zai aure ki? Sayyada". Na amsa. Ya ce"Ni ne fa, Saddam ɗinki ne, ban yi zaton zan roƙi wannan ɗan abun ki ƙi yi mini ba, har kin manta soyayyarmu? Har kin manta irin zaman da muka yi? Kin manta irin abubuwan da kika yi min na yafe miki? Me zai saka na ƙara son zama da wacce ta so kashe ni idan ba ƙauna ba? Haba Sayyada ki yi min adalci mana, idan kin zubar wata nawa ne mun yi aure kin samu wani cikin? Ina da kishi a kanki, ba zan so ki samawa yaranmu 'yan uba ba, don Allah Sayyada ki amince, kar ki raba mu ki haramta mana kasancewa ma'aurata a karo na biyu, na yi miki alƙawarin farinciki har ƙarshen rayuwarki". Jikina duk ya mutu, idan akwai abin da na tsana bai wuce Sadam ya tuna min na caka masa wuƙa ba, na share hawayen da ya sakko min na ce"Na amince Sadam indai hakan zai saka ka yarda da ni". Ya ce"Alhamdulillah, yanzu ya kenan? Zan san yadda za a yi a samu maganin daga hannun Safna, gobe in sha Allah zan kawo miki, tun da bai kai wata biyu ba ba zai wani yi wahalar fita ba". Na ce"To Allah Ya kaimu" Muka yi sallama, sai na ji raina fess. Washegari kuwa sai ga kiran shi da azhar, ya ce "Maganin ya zo hannu fa My Baby" Gabana ya faɗi, saboda har zuciyata ina son abin da yake cikina, ina so na haihu, kawai dai ba ni da wani zaɓi ne, saboda ina fargabar idan ya kufce min gidan wa kuma zan faɗa, na ce"Da sauri haka? Amma ya aka yi ta yarda ta ba ka?" Ya ce"Sakawa na yi ta rubuta min, na ce mata wani abokina ne matarsa ta samu ciki kuma ɗansu watansa biyu, shi ne za a cire cikin". Na ce"Ma sha Allah". Ya ce"Ya za a yi ki fito ki karɓa?" Na ce"Zan ce zan je gidan su Anisa, sai mu haɗu a hanya". Ya ce"Ok, to bari zuwa la'asar ko?" Na ce"Allah Ya kaimu". Tun da muka gama wayar na ce da Mama zan leƙa gidan su Anisa, ta ce"Sayyada yawo fa ba naki ba ne". Na ce"Wallahi iya nan kawai zan ke, kuma ba zan daɗe ba". Ta ce"A dawo lafiya". Kamar yadda muka tsara, haka na fita bayan ya ce min ya kusa ƙarasowa, muka tsaya a hanya ya ba ni maganin, har da gashasshiyar kaza da lemo, na karɓa na yi godiya, ba mu wani tsaya ko gaisawa ba kawai ya shiga mota ya tafi saboda tsaro, haka na sunƙe ledar a hijjacina har na koma gida, dab da magriba, sai da na idar da sallar isha'i na zauna na ci kazar a ɗakina, ina fargabar kar Mama ta jiyo ƙamshi, bayan ta ishe ni, na sha lemon, na ɗakko maganin, na tsaya ina kallon shi hannuna a kan cikina, ina jin son abin da yake cikina, a ce da kaina zan kashe ɗana? Ɗan da nake burin a ce yau na ajiye shi a doron duniya? Anya kuwa? Hawaye suka fara sakko min, a fili na furta zan yi komai ne ba da son raina ba, sai don son gyara gobena". Na ɓallo maganin, na ɗauki ruwa, salatin da Mama ta rafka tare da shigowa ɗakin bagatatan shi ya dakatar da ni, har na saki ruwan hannuna da maganin cikin nuna rashin gaskiya, ta ƙaraso ta ɗauke ni da mari tass, na dafe kuncina na fara kuka, ta ce"Ashe ba ki da hankali Sayyada? Yau na tabbatar da wautarki mai girma ce". Cikin ƙarfin hali na ce"Mama me na yi?" Ta ce"Ubanki da uwarki kika yi, kin yi zaton ban san duk takunki ba? Kin yi zaton don yanzu kin girma na daina rainonki da kulawa da amanar Allah? To duk wayar da kika yi da Sadam jiya a kunnena kika yi, na taho zan kawo miki zogale na ji kina waya na dakata, na ji komai na ji shirinku, amma Sayyada kin ba ni mamaki wallahi, me yasa yaran ya zu ba kwa yi wa iyayenku adalci? Sayyada me kike nufi? Sadam ta fi miki kowa kenan? A tunaninki wannan soyayya ce? Duk mai sonki yana son farincikinki bari ki ji, Sadam ba ya sonki, kuma ko soyayyar juna za ta kashe ku ba za ki aure shi, na bar hanyarsa har abada ni ma, ba na tare da aurenku ko bayan raina, daƙiƙiya kawai wacce ba ta san ciwon kanta ba". Daga haka ta kwashe maganin, kazar, da wayata ta bar ɗakin, ta bar ni ina gursheƙen kukan nadama da tashin hankali. Na daɗe ina yi kafin na tashi na shiga ɗakin nata, na durƙusa ina hawaye na ce"Don Allah Mama ki yi haƙuri ki yafe min, na yi kuskure, wallahi sharrin shaiɗan ne, ba zai sake faruwa ba". Mama ta ce"Ke da shi ne shaiɗanun, kar ma ku ƙalawa shaiɗan sharri, shi wannan Saddam ɗin har ya fi shaiɗan, ban da yana nufinki da sharri zai ƙi son ki haihu ki samu jininki ne? Ke jahilar ina ce kina cikin idda kin san ko yau mijinki ya ce ya mayar da ke kin maidu kuma wai ki fara kula wani banza wanda ba ya son cigabanki?" Na sake rushewa da kuka na ce"Ki yi haƙuri Mama don Allah, wallahi ni ma ina so na haihu dama". Ta zaburo ta ce"Tashi daga nan kafin na mangare ki, wallahi kin ci albarkacin abin da yake cikinki, da yau sai na yi miki dukan tashi ki sha kunu a cikin gidan nan". Na ce"Don Allah ko ba za ki haƙura ki yi min hukunci ke kaɗai, don Allah kar ki faɗawa Baba, korata zai ƙara yi, na ji na haƙura da auren Sadam, amma don Allah kar Baba ya ji". Mama ta ce"Ya zama dole ya ji, idan kina tsoron shi ai ba za ki aikata ba, kuma da kaina zan je gidan su Sadam ɗin na sanarwa iyayen shi a yi mana tsakani, a kan shi rayuwarki ta lalace har yanzu kike cikin walagigi". Da sauri na ce"Don Allah Mama ki yi haƙuri, wallahi tsautsayi ne, na yi na farko na yi na ƙarshe". Mama ta yi banza da ni, na ci kuka na ƙoshi, sai da na ji dawowar Baba sannan na tashi na fito daga ɗakin, na saita kaina na ce"Baba sannu da zuwa". Ya ce"Yawwa, Sayyada ƙalau ko?" Na ce"Lafiya lau". Na shiga ɗakin har da saka sakata, saboda kawai gani nake yana shiga ɗakin Mama za ta faɗa masa, shi kuma shigowa ɗakina kawai zai yi ya rufe ni da duka, amma sai na ji shiru duk da haka ban nutsu ba, ga wayata da Mama ta karɓe, na tabbata Saddam zai neme ni. Da gaske na yi nadama ba a iya fatar baki na faɗawa Mama ba, sai yanzu ma na ga wautata, na dinga istigfari, na yi niyyar zan haihu ko da ba zan sake samun wani mijin aure ba har abada, zan zauna na raini ɗana ko 'yata. USTAZ Tun da yana son ya tsira da mutincinsa sai ya haƙura da zuwa gidan su Sayyada, a ransa ya ce kuɗin zogalensa ma ya huta. Yau ya je zance gidansu Rauda, yana ta ɗari-ɗari yana ganin matsayinsa bai kai ba, ita kuwa sai nan-nan take yi da shi, Allah ne ya ɗora mata soyayyar shi, sai da ta gaida da kowa na gidan, suna zaune a ɗakin baƙi yana ci abinci, yana yi mata wa'azin rashin amfanin cin abinci mai yawa, ba tare da ya ankara da yadda yake ta komawa cikinsa abincin ba, bayan ta gama cin abinci ta ce"To yanzu dai da gaske ka shirya auren ko? Don na san Abba yana dawowa idan ya ji ka fara zuwa zai ce to ka fito". Ustaz ya kalli Rauda, ba wata kyakkyawa ba ce, amma 'yar gayu ce, hutu da gayu suna magana a jikinta, fatar nan luwai-luwai ko ba taɓa ta ya san za ta yi laushi, baƙa sai sheƙi take yi, ga ta da cikar halitta, don a wannan zaman da suke yi ma daurewa kawai yake yi, domin ya san tilas ya yi wankan tsarki idan ya koma gida, ta ce"Ka yi shiru kana ta kallona". Ya sauke ajiyar zuciya ya ce"To ai Raudatu ni tunanina ɗaya, kin ga fa ni talaka ne, ta yaya zan fara ajiye ki a gidana wanda zai kasance tamkar kurkuku a gareki? Ina nufin saboda ƙanƙantarsa da kuma ƙarancin kayan more rayuwa". Ta yi murmushi ta ce"Malam ni ai kai nake so ba wasu kayan more rayuwa ba, indai za ka aure ni ka ba ni kulawa da soyayya ai ko a daji zan zauna". Ustaz ya ce"Ai kuwa indai soyayya ce an zo wajen, za ki ga kulawa gaskiya, ina ga ma har sai ta yi miki yawa". Ta ce"Dama kulawa tana yawa ne?" Ya ce"To ni dai haka matan da na aura suke cewa, su na dame su, kuma na ga sai kana son mace da kuma sanin darajarta ne zai saka ka dinga yawan don kasancewa da ita? Ba haka ba ne Malama Rauda?" Ta ce"Hakane mana, ai kuwa ba su da hankali, to ni yanzu idan an yi auren sai ka haɗa duka da kulawar da ka yi niyyar ba su, ka ba ni, Ni kam ko ba za ka dinga fita aiki ba sai zama tare da ni ina buƙatar hakan". Ya ce"Alhamdulillah, to yanzu ya kenan?" Ta ce"Duk yadda ka ce". Ya ce"Zan je na fara tara abin da ya samu sai a san ko wata nawa za a saka ranar ko?" Ta ce"Ni fa zan iya yafe maka lefen ma, ko kuma na ba ka kuɗin ka yi don kar ya zama abun magana". Ustaz ya ce"Lala-lala, wannan ba zai faru ba, zan yi iya ƙarfina bi izininllah". Suka cigaba da fira, sai da ya ji yana neman rasa nutsuwarsa gabadaya sannan ya yi mata sallama ya tafi, ransa fess yana ta hango yadda daren farkonsu zai kasance idan Allah Ya yi. 08028966015 [27/10, 8:06 pm] Sadiya Abdulrazak: 29 Kai tsaye gidan iyayen shi ya wuce, ya yi musu bayanin aure zai yi, ga kalar wacce zai aura kuma, babar shi ta fara faɗa tana nuna masa Rauda fa ba sa'ar auren shi ba ce, yana ta nuna mata ai ba za a samu matsala ba tun da ita ta ce tana son shi, ta ce"aAnya kuwa Ashiru? Har yaushe aka yi na Sayyada ka manta? Aure biyu duk ba ka yi dace ba, ya kamata ka haƙura ko kuma ka fara bincikawa ka ji mai irin larurrka, yanzu za a fara ƙirga maka aure fa, ana cewa auri saki ne da kai, nan gaba sai ka ga ka ƙi auruwa". Ya ce"Zan faɗa mata in sha Allah". Ta ce"Ni dai wallahi don ka dage ne Ashiru, amma yaran masu hannu da shunin nan idan suka auri talaka yawanci ana samun matsala, sai ka ga ta zama ita ce mijin ita ce mai tsara komai". Ya ce"Umma ita fa Rauda ba ta da wannan halin, tana da kyakkyawar zuciya, na faɗa miki fa silar wa'azina da ta ji yasa ta kamu da sona, tana da tsoron Allah, tana da gudun duniya, in sha Allah ba za ta min irin wannan halin ba, kuma ai an ce tuwon girma miyarsa nama, don haka dole zan saki aljihu na dinga wadatata da kwatankwacin irin abin da take ci a gidansu, duk da ba zai yiwu na iya sak na gidansu ba, amma zan ƙoƙarta". Ƙarshe dai da ta gaji ta ce Allah Ya ba da zaman lafiya. Bayan kwana biyu mahaifin Rauda ya kira Ustaz, ya je gabansa sai faɗuwa yake yi, suka gaisa a mutunce, da alama yana da kirki, ba shi da halin raina arziƙin talaka, ya ce"Malam Ashir ko?" Ustaz ya ce"E Abba, haka sunan yake". Ya ce"Rauda ta sanar da ni kun sasanta kanku, kuma na yi nawa binciken a kanka, bincike ya tabbatar da aurenka biyu, babu ɗa ko ɗaya, hakane?" Ustaz ya ce"Hakane, ita ta biyun ba a daɗe da rabuwa ba ma, don a yanzu haka ma zancen da ake yi, ba ta gama idda ba, to ka san ita iddar macen da ta kasance mai ciki bi ma'ana juna biyu shi ne ta haihu, ko yanzu aka sake ta bi ma'ana aure ya mutu, bayan minti ɗaya sai Allah Ya kawo haihuwa to fa ta kammala iddarta, kamar yadda ko cikin jikinta na kwana ɗaya ne, idan aure ya mutu sai ta haihu za ta gama idda, bi ma'ana sai ta yi wata tara, to hakan ne ya faru da ita tsohuwar matata Assayyada, ni ban san ma ta samu rabon ba, sai bayan an yi shi ɗalaƙin bi ma'ana sakin, sannan sai ciki ya bayyana, yanzu haka dai ina tunanin ya cika wata biyu, ka ga kenan ba ta kammala iddarta ba, wannan bayanin na yi ne domin gyara ko ƙara maka sani a kan maganar da ka ji a gari ta cewar ba ni da ɗa, bi ma'ana na haska maka ba wai haihuwa ce ba na yi ba, yanzu haka ɗana yana nan yana rayuwa a cikin tsohuwar matata, rabon ne dai a nesa shi yasa matar ta farko ba ta samu ba". Abba ya ce"Ma sha Allah, Allah Ya raba lafiya". Ustaz ya amsa da amin. Abba ya ce"To amma ina son jin dalilin mutuwar auren naka, tun da duk bincike ya nuna ba a wani yi dogon zama ba". Ustaz ya gyara zama ya ce"To Abba shi lamari na aure rai ne da shi, Allah ne shaidata duk macen da zan aura ina aurenta ne da zuciyata ɗaya, da kuma yaƙinin zan rayu da ita har ƙarshen rayuwata, amma sai dai kana taka Allah na tashi, ta Allah ita ce gaskiya, tsakani da Allah ba ni da wata matsala, kawai dai rashin dace ne, ita ta farkon ta raina samuna ne, ita kuma ta biyun nan dama ba auren soyayya ba ne, mahaifinta ne ya ba ni ita, to ashe ba ta sona, ta ƙi kwantar da hankalinta, ƙarshe dai shi mahaifin nata da kansa ma ya ce sai na sake ta, wallahi Abba ban so haka ba, don sai da suka kai ni kotu ma sannan na yi sakin nan, to ka ji dalili". Abba ya yi shiru yana nazari, kafin ya ce"Mene ne sana'arka?" Ustaza ya ce"A kasuwa nake, 'yan shadda, kuma ni ma yaron shago ne, amma dai Alhamdulillah ni babban yaro ne, kuma ana samu daidai gwargwado". Abba ya ce"Ma sha Allah! To ni dai ba na yi wa yarana dole, ba na kuma auren haɗi, kowacce ina ba ta dama ta nemo wanda take so da kanta, domin a samu zaman lafiya bayan auren, Rauda ta ce kai ta zaɓa, ta ce ta ji ta gani za ta aureka, saboda haka ka shirya?" Ustaz ya ce"E to, ba na ce na shirya ba ko ban shirya ba, a zahiri na shirya ko a yau ma idan ta kama za a ɗaura aure, to amma sauran hidindumu ne dai za su ɗan ja lokaci, kasancewata mai ƙaramin ƙarfi kuma zan auri buduruwa irin Rauda, dole akwai shiri na musamman". Abba ya ce"Ta faɗa min ba ka da ƙarfi, kuma kai take so na kuɗinka ba, saboda haka indai akwai sadaki ka kawo kawai a ɗaura aure, sauran kayan duka ba wajibi ba ne". Ustaz ya ji kamar ya tashi ya kama rawa don daɗi, ya ce"Alhamdulillah, ma sha Allah, na gode sosai Abba Allah Ya saka da alkhairi". Abba ya ce"Babu komai, sannan har gidanka an nuna min, sai dai gaskiya gidan nan ya yi wa Rauda ƙanƙanta, ba wai na raina maka ba ne, amma idan ka duba inda aka haife ta ta girma, bai kamata a ce ta koma rayuwa a ƙaramin gida irin wannan ba, tabbas za ta takura". Ustaz ya sunkuyar da kai ya ce"Hakane Abba, dama har da wannan tunanin ma ya sa na nuna mata ba mu dace da juna ba". Abba ya ce"Babu damuwa ai, akwai yadda za a yi in sha Allah, Rauda ita ce autata, duk na aurar da 'yan'uwanta, kuma Alhamdulillah sun yi aure wasu a inda ya fi inda suka taso, wasu kuma a daidai da shi, don haka don dai Rauda ita kaɗai ba za a ƙi sama mata mafita ba, zan iya ba ka aron gidana sai ku zauna a ciki har zuwa lokacin da za ka mallaki wanda ya fi wancen naka ɗin, sannan zan ɗora ka a wani ɓangare na kasuwancina, yadda za ka samu cigaba kai ma har ka dogara da kanka". Ustaz ya ce"Na gode sosai Abba, Allah Ya saka da alkhairi, ya ƙara girma". Abba ya ce"Babu komai, wanann ai yi wa kai ne, fatana dai ka zama mai riƙe amana, sannan ka riƙe Rauda riƙo na gaskiya da adalci, in sha Allah babu abin da ba zan yi maka ba, ai surukinka ɗanka ne". Haka Ustaz ya bar gidan cike da farinciki, kamar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha, a ransa kuwa rayawa yake lallai mahaƙurci mawadaci, har ya hango shi a babban gida, a luntsumemiyar katifa, a ranar ya so faɗawa Rauda shi hariji ne, amma ya fasa gara ya bari abun ya kankama, don shi yana jin ma zai iya canza kansa idan ta nuna ba za ta iya zama da hariji ba, ya haƙura kawai ko da sau biyu a rana take ba shi ya gode Allah, tun da har ita ce silar arziƙinsa ba zai bari wannan damar ta wuce shi ba, a fili ya furta "Alhaji Ashiru ga kuɗi ga Rauda". Dubu ɗari biyu ya tanada zai ba da sadaki, dubu ɗari tashi, ɗari kuma bashi ya ci, sati uku da zuwan shi gidan aka ɗaura aure, kasancewar Ustaz ya gama kashe Rauda da wa'azi da nasihohi a kan gudun duniya, kuma dama can ita ma tana da gudun duniya, shi yasa babu wani party da za a yi, kawai tarewa za ta yi, amma ta ce sai nan da sati biyu idan kammala shirinta. Ranar da aka ɗaure Ustaz ya rasa ina zai saka kansa don daɗi, takaicinsa ɗaya ba yau za ta tare ba, tsakani da Allah ya matsu, ba don kar ta ga zalamarsa ba da ya roƙe ta su je gidan nasu ta rage masa zafi ko babu katifa, amma dai ya daure sai dai ya yanke ranar ya shirya zai faɗa mata shi wane ne. Wajen tara na dare suna yin waya, ya ce"Amaryata". Ta ce"Na'am angona". Ya ce"Ina son mu yi wata magana da ke, akwai wata matsala da na manta ban faɗa miki ba, kuma babba ce sosai, ina fargabar ma kar ki ji ki fasa auren". Ta ce"Subhanallah, mene ne?" Ya ce"Don Allah ki yi min adalci, wallahi ina ƙaunarki, ni ma ba yin kaina ba ne, haka Allah Ya ƙaddara min, ke ce ƙarshen hope ɗina, idan kika guje ni na san shikenan kuma, ba baki nake yi wa kaiwa ba, ba zan sake samun mace ta gari ba". Duk ta rikice ta ce"Don Allah ka faɗa min Sweetheart, mene ne wai? Duk ka tsorata ni". Ya ce"To a gaskiya ni ba normal mutum ba ne kamar kowa, ni hariji ne, bi ma'ana mai yawan buƙatuwa, ina da yawan yin sex fiye da zatonki, shin za ki iya jurewa?" Rauda ta yi dariya siriri har da rufe fuska saboda kunyar maganarsa, ta kashe wayar. Ya sake kira ta ƙi ɗauka, sai washegari da ya kira yake jaddada mata, ta ce"Kar ka damu, in sha Allah zan iya". Ita gani take mene ne wani abun damuwa don miji yana yawan yin sex? Sam ba ta san akwai wani hariji ba, kawai a tunaninta yawan yin sex yana nufin shi ɗan soyayya ne, tana da sha'awa mai ƙarfi, don wani lokacin har tana jin kamar ta fara biyawa kanta buƙata, amma da yake ta san illar hakan a addinance da kuma likitance sai take ta haƙuri da fatan Allah Ya kawo mata miji na gari, yanzu ta samu lafiyayye me za ta yi idan ba farinciki ba? Ustaz ya ce"Amaryata kin yi shiru, shin za ki iya da ni? Matana biyu a kan haka suka rabu da ni, sun azabtar da ni, guduna suke su hana ni haƙƙina, don Allah ki zama mai share min kuka a rayuwar aure". Ta ce"To ni ban san amsar da zan ba ka ba ne, kawai dai zan ce maka na gode Allah da ya ba ni lafiyayye miji, ka saka a ranka kukanka ya zo ƙarshe daga kaina". Ustaz ya yi tsalle ya dire, farinciki kamar ya kurma ihu, ya dinga jero hamdala yana yi mata godiya da faɗin"Indai ni ne mijinki Rauda na ɗaga miki ƙafa ki shiga Aljanna, ina kyautata zaton za ki zame min Raudatul dunya, Allah Ya miki albarka matata". Ta dinga dariya tana cike da farinciki, Allah ne ya ɗora mata soyayyar Ustaz, kuma ga shi ya cika mata burinta ya zama mijinta, sannan tana son miji mai ba da kulawa da nuna soyayya, da alama ta yi dace burinta ya cika, ta gode Allah da ya haɗa Ustaz da wawayen mata a baya, inda sun san abin da suke yi ta tabbata da yanzu ba su yi wasarere da shi ba har ta tsinci dami a kale". Ya ce"Anya zan iya jiran lokacin tariyar nan kuwa? Don Allah a ɗan rage kwanakin". Ta ce"Gaskiya ba sai an rage ba, kuma ma ai ƙaruwarka ce, kai fa nake yi wa gyaran". Ya ce"Gyara ko a gidanmu ai za ki yi". Ta ce"A'a ka bari a hakan kawai kamar fa yau ne". Suka yi sallama kowanensu cike da farinciki, bacci yana ɗaukar shi ya fara mafarkin ga shi ya kasance da Rauda. SAYYADA Wani irin yanayi na shiga na ƙunci da baƙinciki, ga kuma fargabar irin yadda Sadam zai kalli lamarina, na saka damuwa a raina na yi ta zaman kaɗaici, Mama kuwa ta ba wa banza ajiyata, gaisuwa ce kawai take haɗa mu, sai dai idan tana yin aiki na je na karɓa wataran ta ba ni, wataran ta ƙi sakar min, Baba kuwa da bai san abin da na aikata ba, ƙalau muke da shi, kullum zai shigo min da leda, kayan marmari ko ɗan nama, sannan kullum zai kawo zogale ɗanye na dafa ko kuma dafaffe, na yi kwaɗon shi, cikin wata ɗayan ko da wasa ban fita ba, ga shi Mama ba ta ba ni wayata ba, kuma ban tambaye ta ba, akwai ranar da ta tafi unguwa, na shiga ɗakinta, na dinga bincike, da ƙyar na gano wayar, sai dai na yi saranda, ganin layukan cikin wayar an tattauna su an watsa su cikin ledar da aka ƙulle wayar, takaici ya saka ni fashewa da kuka, na san Saddam yana can yana ganin na yaudare shi, da wane idon zan kalle shi? Duk da dai ta wani fannin ina farinciki da rashin zubewar cikin. Sanda na shiga wata na biyu da faruwar wannan abun, watarana Mama ba ta nan na shiga maƙota na ari waya, hannuna yana rawa na saka lambar Saddam, plashing ma na yi don babu kati a wayar, na yi sa'a ya kira, na shiga gidanmu na rufe ƙofa har da saka sakata, na shiga ɗaki na kwanta sannan na ɗaga wayar. "Hello, Hello da wa nake magana?" Muryarsa ta sa na ji wani rauni ya rufto min, zuciyata ta fara kumburowa, kawai na saka kuka, da kukan ya gane ni ce, ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ya ce"Ba ki da abin da za ki ce min Sayyada, kin bayyana mini komai a aikace ai". Ya katse kiran, na tashi zaune na sake yi masa plashing, bai kira ba, ai kuwa na dinga jera masa babu ƙaƙƙautawa, sai ga shi ya gaji ya kira, ya ce"Sayyada me kuka za ki ce min? Ni dama na san tun da kika tsane ni ba za ki ƙara sona ba, saboda ba ki da yafiya, ba ki da adalci, amma abin da ya ba ni mamaki shi ne me yasa za ki yaudare ni ki yi min ƙarya? Haka kika tsara ko? Shikenan ki je ki haihu Sayyada, ki koma gidan harijin mijinki ya dinga yi miki abin da ya sabar miki da shi, wanda ni ba zan iya ba, tun da ni ba doki ba ne, ba kuma jaki ba ne, dama na san kina son shi dole za ki koma, shi yasa kika ɗauke ni wawa wanda ban san me nake yi ba, ki je ki haihu, ki haifi yara dubu ma Sayyada, Allah Ya sauke ki lafiya, amma bari ki ji na faɗa miki, ba ki da adalci, ba ki da kirki, ba ki yi min adalci ba, kuma duk ranar da kika sake kirana ko kika gan ni a hanya kika nuna kin taɓa sanina, za ki sha mamakin wulaƙancin da zan tata miki". Ya kashe wayar, na ajiye wayar hannu na rushe da kuka, na kifa kaina a cinyata ina ta yi, sai da na yi mai isa ta sannan na fita na wanke idona na mayar da wayar, na dawo na kwanta, zuciyata tana ta zafi, wai da me zan ji ne? Ga Mama tana fushi da ni, ga shi wanda ya ja mini fushin nata shi ma ya ƙi fahimtata, ina suke so na saka kaina ne? Na shafa cikina na ce"A kanka ne komai yake faruwa, amma ba ina nufin laifinka ba ne, zan haife ka in sha Allah, ba zan sake yunƙurin kashe ka ba, tun da wanda na so yi domin shi bai yi mini yardar da zai tantance abin da zan iya da wanda ba zan iya ba, Astagfirullah Allah". 08028966015 [28/10, 7:49 pm] Sadiya Abdulrazak: 30 USTAZ Saura kwana biyar Rauda ta tare ta ce Ustaz ya zo su je ya ga gidan da za su zauna, ya tafi yana ta rawar kai, direban gidansu ne ya kai su, suka shiga, shiga ne madaidaici, mai yalwar tsakar gida, babban falo ne da ɗakuna guda uku a ciki, sai kitchen da ban ɗaki, sannan kowane ɗaki a kwai banɗaki a ciki, ga kuma dining room a falon, nuna masa gidan take shi kuwa ita yake kallo da marari, ba ta gidan yake ba, ba ta ankara ba ya ji ya rungume ta, ta runtse ido suna sauke ajiyar zuciya a tare, ya ce"Amaryata sai nuna min gida kike yi, alhalin kin san ke na fi buƙatar ki nuna min kanki ba gida ba". Ta ce"To kwana nawa ya rage, idan ka yi haƙuri ai za ka gaji da ganina ma". Ya ce"Wallahi ba zan gaji da ganinki ba, da kin san yadda na matsu mu tare da kin taimake ni yanzu, za ki iya?" Ta ce"Ina na matsu, amma dai ka bari na tare ɗin, sai ka fi samun nutsuwa". Ya marairaice mata yana ta roƙonta, har ta amince aka yi romance a tsaye kamar dole, Ustaz duk ya firgice amma ta ƙi yarda a je ga babban lamarin, ta ce babu katifa, haka suka koma gida a birkice suna cike da ɗaukin juna. Ana gobe za ta tare aka yi walima, malamai suka yi wa'azi, aka ci aka sha, aka tsantsara jere, washegari da daddare wajen ƙarfe takwas an gama komai, da motocin gidansu ma aka kaita ɗakinta, yayin da Ustaz ya haɗa nashi kayan shi ma, ya buga babur ɗinsa ya tafi gida amarya, tuni ya saka 'yan haya a gidansa, da kuɗin ma ta samu wanda zai yi 'yan hidimominsa, a hanya ya tsaya ya sayi kaji manya guda biyu, don ya san Rauda ba wacce zai kaiwa ƙaramar kaza ba ce, yana hanya ta kira shi, tana marairaicewa ta ce"Wai kana ina ne? Kowa fa ya watse sai ni kaɗai". Ustaz ya ce"Ina hanya matata, me kike ci na ba ka na zuba?" Sanda ya ƙaraso tana falo a zauna, ya ƙarasa da farinciki yana gyaran murya, ya zauna a kusa da ita ya shiga jero godiya ga Allah da nuna farincikin da yake ciki, Rauda tana jin daɗin yadda Ustaz yake ta rawar jiki a kanta, ita kam yau burinta zai gama cika, za ta haɗa shimfiɗa da wanda ta fi so a duk duniya, kuma a matsayin ma'aurata, ya ce"Kin yi shiru sai murmushi kawai kike yi, anya farincikinki azeemun ne kuwa? Ni fa ji nake kamar yau na fara yin aure". Ta ce"Naka ne ya fito sarari, amma da zan iya buɗe maka zuciyata da za ka gane nawa ya fi naka sau dubu, ina sonka Malam, ina fatan ka riƙe ni da amana mu zauna lafiya har ƙarshen rayuwarmu". Ya ce"In sha Allah za ki same ni mai adalci a zamanmu, amma ni dai wannan farinciki da kika ce ba zan yarda da shi ba a fatar baki, sai na gani a aikace, bi ma'ana nuna farincikinki a kan gado shi ne farinciki na zahiri". Ta rufe fuska tana murmushi. Ya ce"Amarya tashi za ki yi mu yi alwala mu yi sallah, saboda idan aka ƙara lokaci ina kallonki komai fa zai iya faruwa, kuma kin ga sunna ce mu fara gabatar da sallar godiya ga Allah". Ta ce"To" bayan sun yi sallah suka ci kaza, ya shiga wanka ta fito ta yi shigar bacci, tana zauna a bakin gado shi ma ya shiga wankan, ya fito jikinsa har rawa yake yi ya matso kusa da ita, idanunsa kawai ta kalla gabanta ya fara faɗuwa, a matsayinta na buduruwa wacce ba ta taɓa samun kusanci irin haka da wani namiji ba, idanunsa duk sun canza launi yana yi mata marayan kallo mai kashe jiki ya ce"Ina yi miki barka da shiga sabuwar duniya amaryata, duniyar Ustaz ɗinki mai ƙaunarki, ina fatan ki cika alƙawarinki na zama mai share min hawaye a zamantakewar aure, shin kin shirya karɓata?" Ta marairaice ta ce"Da dai ka bari sai gobe, wallahi a gajiye nake, jikina duk ciwo yake" Ustaz ya riƙo hannunta duka biyun ya ce"Subhanallah! Ban so jin wannan kalami daga bakinki ba, gajiyarki a wannan daren daidai take da kassara lafiyata, Rauda da kin san ɗumbin ladan da za ki samu da ba ki furta min kalmar gajiya ba, ko da kuwa kin kai matakin da ba kya iya motsi saboda gajiyar, wannan daren farkon mu ne, shi ne dare mafi girma da tsada a duk tsayin shekarun da za mu yi, kasancewa a daren farkon nan na ranar da aka tare ya fi armashi da ɗumbin lada, daure ki taimake ni ki ba ni haɗin kai na kai ki sabuwar duniya mai cike da farinciki kin ji?" Ta ce"Ni ma na so hakan, amma wallahi na gaji sosai, da gaske ba zan iya ba". Ustaz ya ce"Ai kuwa da sake, a wallahi da sake, bari na faɗa miki gaskiya, ko ba daren farko ba ba zai yiwu a ce wani dare ya zo ya wuce ban raɓe ki ba, gajiyar biki ai ba ta hana angwancewa, ki taimake ni, na yi miki alƙawarin zan wartsakar da ke". Daga nan bai sake ba ta damar cewa komai ba, manyan lamura suka fara gudana, faɗin halin da Ustaz ya shiga ba ya misaltuwa, ku auna da kanku, harijin namiji irin Ustaz ya gamu da cikakkiyar budurwa kuma wacce ta ji gyara ciki da waje, sannan mai son shi wacce ta karɓi abun har zuciyarta da kuma shauƙin abun, ɗan ƙaramin hauka ya yi, don gabaɗaya ya fita hayyacinsa, yayinda Rauda ta yi iya ƙoƙarinta na ganin ta daure ta faranta masa, duk irin azabar da take sha, amma sai dai ina, idan ka gamu da wanda bai iya cin ƙwan makauniya ba to fa duk yadda ka kai ga kau da kai sai ya ƙure ka, tun ba kai awa ɗaya ba ta fara kukan gasken gaske tana faɗin"Na gaji Sweetheart, ya isa haka". Shi kuma kamar ma kurma, don gani yake sai yanzu ne ma aka fara wasan, sam ba ya jin irin kukan da take yi, kamar ya manta wacce ta kasance baƙuwa a lamarin yake tare, ta san ana shan wahala a daren farko, amma ba ta yi zaton abun ya kai haka ba, awa biyu an shiga ta uku amma mutum kamar ƙara masa ƙarfi ake yi, azabar da take ji tana ƙaruwa, sai da ta ga da gaske neman rayuwarta yake yi sannan ta fara ihu na gaske tana dukansa da kiran "Malam Ashiru ya ishe ka haka, kashe ni za ka yi?" Allah ne Ya dube ta ya ba ta dabarar gasa masa cizo a kafaɗarsa, ta ƙi saki kamar za ta yage naman jikinsa, sai a lokacin azaba ta dawo da shi cikin hayyacinsa, ya ɗaga ta da sauri yana karanto Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yadda take fitar da numfashi yana sama da ƙasa ya tsorata shi, ya ɗago ta yana cewa"Ki yi haƙuri Rauda, ke ɗin ce kika gigita ni wallahi, sannu". A hankali ta ce"Ka dafa min ruwan zafi". Ya ce"To, amma bari na yi wanka tukunna". Ya tafi banɗaki ya yi wanka, yana jin sam bai gamsu ba, ya tafi dafa ruwan, a maimakon ya dora sai ya tsaya kallon kitchen ɗin, daɗi ya rufe shi ganin uwar garar da aka yi mata, kayan abinci jibgi guda, a fili ya furta"Alhamdulillah, ni da fita kasuwa sai nan da sati biyu". Ita kuwa Rauda hawaye ne yake ta sakko mata, ba ta taɓa zaton haka za ta tarar a daren farkonta ba, daren da aka ce yana cike da farinciki da samun nutsuwa ita kam na azaba ya zame mata, shi ya yi mata wankan, yana jin kamar zai koma mata, daurewa kawai ya yi, ya taimaka mata ta shirya ta kwanta, ya yi mata addu'a ya shafa mata, yana cewa"Rauda lamarin nan fa sai fa kin daure, shi yasa idan aka aurar da yarinya za ki ji ana cewa girma ya zo, to fa wannan shi ne girman, kuma ladan za ki dinga dubawa ba wahalar ba, na yi miki tausa?" Ta ce"A'a ba na so". Ya shimfiɗa sallaya ya fara sallah, ita kuma ta yi baccinta, can cikin baccin ta, shi ma bai daɗe yana sallar ba ya zo ya kwanta. Can cikin bacci wajen ƙarfe uku ta ji ana shafa jikinta, na farka ta yi juyi ta matsa daga kusa da shi, don abun ba hauka ba ne kuma, ya matsa a kunnenta yake cewa"Ai kin huta, taimake ni mu ƙarasa, wallahi kamar ban yi komai ba nake ji na, ba ki bari na samu nutsuwa ba ɗazu". Gabanta ya ba da rass, ta ce"Ban gane ba ka samu nutsuwa ba, duk wannan wahalar da ka ba ni?" Ya ce"Yi haƙuri ki daure dai". Ya fara ƙoƙarin raba ta da rigar jikinta, ta tashi zaune tana cije baki ta ce"A'a wallahi ba zai yiwu ba, indai kuma ba kashe ni kake son yi ba". Ustaz ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kaico! Subhanallah, wato Rauda ban taɓa zaton jin wannan kalami daga bakinki mai albarka ba, ya ina yabonki sallah za ki kasa alwala? Shin kin manta na faɗa miki ni hariji ne? Kin manta alƙawarin da kika yi mini na za ki kula da ni ki share min hawaye? Wallahi wannan shi ne hawayena, matuƙar za ki dinga amsa kirana duk lokacin da na buƙata to kin share min hawaye, kuma kin zama sarauniyar zuciyata, kin mallake ni ma sai yadda kika yi da ni, don ki taimaki masoyinki mijinki Rauda". Ta share hawaye ta ce"Na gaji ne, ba ka san yadda nake ji ba, ba zan iya ba a yau dai, amma idan muka saba zan yi iya ƙoƙarina na ga idan zan iya sabawa". Ya ce"In sha Allah za ki saba, amma don Allah yanzu ki ɗan rage min". Ta ce"Wallahi ba zan iya ba". Duk nacinsa haka ya haƙura ya rabu da ita, da asuba yana dawowa daga masallaci ya shiga yi mata magiya, a dole ta ba shi, nan ma da ƙyar ta yakice shi, ta narke ta ce ba za ta iya yin aikin komai ba, Ustaz ya ce la ba'asa, ya shiga kitchen ya dafa musu shayi, ya tambaye ta da me za ta karya, ta ce danlali, ya soya shi da yawa, sannan ya ɗakko butter da biredin fa ya taho da shi jiya, ya haɗa komai ya kai dining, sannan ya je ya taho da ita tana ta narkewa, a baki ya dinga ba ta har ta ce ta ƙoshi, ya ɗauke ta ya mayar da ita ɗaki ya kwantar, tana cewa"Ni da ka bar ni a falo". Ya ce"A'a, gara nan ɗin, tun da ai kin ga share falon zan yi idan na gama". Ya fita yana murmushi, a ransa kuwa ya yi haka ne don kar ya karya a gabanta, don ya san ta'asar da zai yi wa kayan shayi, Ustaz ya zauna ya zuba shayi a kofuna biyu, kowanne ya zabga madara da milo, mai shan shayi da sugan naira ɗari su biyu sai ga shi ya zabga wanda bai san na nawa ba ne, shayi ya yi kauri murtuk, ya saka shi a gaba, tass ya cinye dankalin duk yawanshi, ya ci rabin ƙaton biredin, ya yi hamdala gumi yana karyo masa, ya ce"Ma sha Allah, to fa indai aka cigaba da tafiya a haka la shakka yanzu zan murmure na zama mutum, bi ma'ana duk inda ya komaɗe zai taso, wa man taraka bati siddan". Ya kwashe kanukan ya kai kitchen ya yi wanke-wanke, ya gama ya share ko'ina a gidan ya goge tass, ya zauna yana mayar da numfashi, yanzu kuma babu abin da yake so sai Rauda ta taimake shi, don haka ya tafi ɗakin don gwada sa'ar shi, bacci ya ɗauke ta, ya tuɓe ya hau gadon, yana fara taɓa ta ta tashi da sauri, ta kyaɓe fuska kamar za ta yi kuka ta ce"Wai da wane yaren zan yi maka bayani ka fahimta?" Ya ce"Larurata ba ta jin kowane yare sai na ba da haɗin kai, kuma ai na yi miki bayani". Ta ce"To a gaskiya ba zan iya ba, na gaji, dama haka ake auren?" Ya ce"Haka ake yi mana, ke nufinki hutu kika zo? Da ake cewa aure ibada ne ai wannan ce ibadar, lada ne fa kike samu bila adadin, shin dama akwai wanda zai ce lada ya yi masa yawa ba ya buƙatar ƙari? Daure ki ƙara min kin ji, daga na yanzu zan daure in sha Allah sai kuma dare ko bayan la'asar haka". Haka Rauda ta miƙa kai, duk jikinta ya yi sanyi, yau ɗaya har ta gaji duk yadda take jin sha'awa da zumuɗin abun, ta so ta daure ta rabu da shi har ya samu gamsuwar da yake cewa bai samu ba, amma da ta gaji ta ga ba za ta iya ba dole ta saka masa kuka, ya ƙyale ta. Shi ya yi girkin rana ma, ya dafa musu jollof ɗin macaroni, yana kitchen ɗin ta shiga tana kallon yadda ya zage yana ta aiki, ta yi murmushi tana yi masa vedio a waya, ta ce"Sweetheart ya zama mai girki". Ya yi dariya ya ce"Ai kuwa indai vedio za ki yi min har kya gaji, tun da aikin nan kullum ma ni zan dinga yi miki". Ta ce"A haba dai, mene ne amfanina da zan bar mijina da aiki?" Ya ce"Amfaninki shi ne ki dinga bawa mijinki hakkinsa, indai za ki dinga amsa kirana ba za ki dinga nuna gajiyawa ba to ni kuwa zan iya ɗauke miki duka aikin gidan nan". Ta ce"Zan yi iya ƙoƙarina na gamsar da kai in sha Allah". Ya ce"Alhamdulillah, tabbas akwai alamun ke ce za ki zama mai share min kuka, ke ce matata har gidan aljanna, ina ƙaunarki Rauda, don Allah ki daure kin ji, da sannu ke ma za ki zama harija kin ga abun nema ya samu, sai mu ci karenmu babu babbaka". Suka yi dariya duka, ta ce"Je ka huta kawo na taya ka". Ya ce"Wallahi ba zan huta ba, ki je ki yi zamanki ki ƙara hutawa, yadda za ki ji daɗin bani tallafi anjima". Ta shagwaɓe ta ce"Gaskiya sai gobe". Ya ce"Ai wannan zance ne, na san za ki tausayawa mijinki". Ta koma ɗaki ta zauna, ta kira lambar babbar ƙawarta, wacce ta kasance me aure da yaranta biyu, suka gaisa tana ta tsokanarta amarya, Rauda ta ce"Wai ni Zainab na tambaye ki mana?" Ta ce"To ina jinki". Ta ce"Don Allah dama haka auren yake? A yi ta yin abu babu gajiya, kuma sannan a yi awanni ana yi?" Zainab ta kwashe da dariya ta ce"Ka ga farin shiga, dole a nemi sani a wajenmu, yanzu kin yarda ni yayarki ce ko?" Rauda ta ce"Ba fa zancen wasa ba, don Allah ki ba ni amsa". Zainab ta daina dariyar ta ce"Ai dama a satin farkon nan dole haka za ki gani, tun da yana cikin shaukinki ne, to dole sai kin daure kin yi haƙuri, amma da an kwana biyu kun saba shikenan sai komai ya daidaita za ki ga yana ragewa, ku fara ma fashin kwana ɗaya, daga nan kwana biyu, ni yanzu kin gan ni ma sai mu yi kwana biyar bai taɓa ni ba, idan na tuna lokacin amarci har mamaki nake yi, kamar ba zai wuce ba wallahi". Rauda ta sauke ajiyar zuciya ta yarda ta kuma gamsu, ta ce"To da sauƙi tun da zai wuce, amma fa abun nan babu sauƙi wallahi har na gaji". Zainab ta ce"Kowa da haka yake sabawa ƙawata, daure ki ƙara haƙuri, ki farantawa mijinki, ki sakar masa jiki kar ki bar space ɗin da matan waje za su ƙwace miki shi, don wallahi tun daga lokacin amarcin nan idan kina gudun miji a haka za ku ɗore ba kya sakin jiki da shi, ga kuma mata can a waje da suke nema ido rufe wata ma ita take biyan namiji don haka sai ki yi hankali, ki kama mijinki ram, don dai farko ne yanuy, amma nan gaba za ki daina jin wahalar abun, har ma ki zo kina neman shi". Rauda ta ce"To Allah Ya sa, na gode Zee". Suka yi sallama, ta shiga tunanin anya za ta iya kuwa? Amma tana son mijinta, kuma ta tsani kishiya, don haka dole za ta daure ta yi masa yadda yake so ɗin, sai dai tana fatan lokacin da zai saba ya rage ɗin ya zo cikin gaggawa. Ya gama abinci suka ci, yana ta ba ta kulawa da nuna soyayya, idon a son ran shi ya ƙara abun nan, amma tausayinta yake ji, don haka ya yi wanka ya fice daga gidan, don idan yana ganinta ba zai iya riƙe kansa ba. Da la'asar ta yi baƙi, suka taya ta zama har magriba sannan suka tafi, sai bayan sallar isha'i Ustaz ya dawo gidan, ta tare shi da oyoyo, tana yi masa shagwaɓar ya bar ta ita kaɗai a gida, ya shiga ba ta haƙuri. Ya ce"Me zan dafa mana?" Ta ce"Ai na zata za ka taho mana da wani abun, ni bana cin abu mai nauyi da daddare fa". Ya ce"To ai ba damuwa, kamar me kike so kenan?" Ta ce"Ko irin kazar jiya ce ma, da fruit salad". Ustaz ya ɗan yi jim, kafin ya ce"To zo ki raka ni kitchen ɗin, ki zauna kina yi min fira ina kallonki ina jin daɗi ina yi miki aiki, don wannan abubuwan da kika lissafa duk na iya su, ba dai na ga fruit a firjin ba?" Ta yi murmushi ta ce"Sweetheart yau ka sha aiki fa, Please ka huta haka, gara a siyo ɗin mu je na raka ka". Ya ce"A'a Rauda, wai ya za a yi ga kayan aiki a gida kuma a tafi waje a siya? Wannan fa ya shiga layin almubazzaranci, shi kuma haramun ne". Ta ce"To shikenan dama na ga kamar za ka gaji ne". Ya ce"La ba'asa ban gaji ba, ba damuwa". Ya shiga kitchen, ya ɗakko kaza daga cikin firji ya gyara, a ransa ya a shi wa iyayen Rauda albarka, don wannan aure shi gaba ta kai shi, gara a ce an haɗota da komai har da kayan miya fa, tana zaune tana yi masa fira, tana nuna masa wasu abubuwan ya gasa kazar nan a oven, ya haɗa fruit salad ɗin, ya yi wanka ya bar ta a falo tana ci, bayan ya ci shi ma, ya ce da wa Allah Ya haɗa mu? Aka shiga aiki, tunawa da maganar ƙawarta na cewar na ɗan lokaci ne yasa ta dauriya take iya ƙoƙarinta don ta gamsar da shi, ta saka a ranta za ta daure a gama cinye satin farkon ta gani. 08028966015 [29/10, 8:34 pm] Sadiya Abdulrazak: 31 Ustaz fa aka gyara zama, komai daidai duniya sabuwa, sosai yake ɓarje guminsa da Rauda, ga kuma cima mai kyau, a jikinsa yake jin har ya fara cicciko da komaɗarsa, sosai ya zamewa Rauda bawa, ya yi mata shara, wanke-wanke wanki, girki, sannan ya yi mata wanka, amma soyayyar sam babu armashi a wajenta, saboda wahalar da ita da yake yi, ga shi Zainab sai faɗa mata take ta dinga shan maganin ƙarin ni'ima idan wajen a jiƙe yake za ta dinga samun sauƙi, tana ta sha amma sam babu sauƙi, ƙarshe ta kawo mata gel ta ce ta dinga shafawa a wajen, yauƙinsa zai sa Ustaz ya samu gamsuwa da wuri, amma Rauda sai ta ga nan ma babu sauƙi, kamar ma ƙara tunzura shi take yi. Ba ta gane tana cikin matsala ba sai da suka yi sati biyu a wannan halin babu canjin da aka ce za ta gani bayan sati ɗaya, abun ya fara ba ta tsoro, ya koma kasuwar shi, idan ya dawo kafin sallar magriba sai ya yi, ana sallar isha'i zai dawo ya ɗora, sannan ya yi na safe ko asuba, don taka masa burki ta yi ta ce na safen nan sai dai ya zaɓi ɗaya ko asuba ko safiya, shi ne yake yin ɗaya ya haƙura, saboda haka ta hana shi dawowa cin abincin rana, da safe take saka shi ya zuba a kula ya tafi da shi, don kafin ya tafi kasuwa zai yi girki safe da rana, ita kuma da yamma sai ta yi musu na dare, duk ba ta da nutsuwa saboda takurar nan tashi, ta gaji sosai, har ta daina marmarin abun, a yadda take yawan jin sha'awa kafin aure ta yi zaton abun ba zai gundure ta ba har abada, kawai tana son mijinta ne, ko ta ce ba za ta ba shi ba idan ya marairaice yana ta wa'azi yana kuma nuna shi ya yafe mata ma sai jikinta ya yi sanyi ta ba shi ko da za ta cutu, amma zuwa yanzu ta fara gajiya. Da daddare suna zauna yana cin abinci take cewa"Kaji fa sun ƙara yau, gobe sai ka ƙaro ko guda goma ne, don yau ma pepper soup na yi niyya, to na san ga guda ɗaya ce kazar shi ne kawai na saka ta a miya". Gaban Ustaz ya ba da rass, ya ƙware da shinkafar bakinsa ya fara tari, ta shiga yi masa sannu, ya miƙa masa ruwa, ya sha ya sauke numfashi, ya cigaba da cin abincin, ta ce"Kuma dankali da doya ma sun yi ƙasa, dama ka ga kai ne me cin doya, sai kayan shayi ina ga bai fi saura na gobe ba". Ustaz ya yi shiru ya ma ɓata rai kamar ba ya jinta, ta ce"Sweetheart magana nake yi fa". Bai kula ta ba, sai da ya gama cin abincin, ranta ya ɓaci ta juya masa baya tana danna wayarta, ya sha ruwa ya yi gyaran murya ya ce"Rauda shin manta yana daga laduban cin abinci idan ana ci a yi shiru ba a magana? Wannan ba halin mace ta gari ba ne a ce miji yana cin abinci tana kawo masa wasu ƙorafe-ƙorafe da uzururruka marasa dalili". Ta ce"Ka yi haƙuri". Ya ce"Ya wuce ai". A ransa kuwa tunani yake yi shi ta ina zai ce zai iya siyayyar duk irin ta'adin abinci da ake yi a gidan nan? Gaskiya dole a canza zama, washegari da ya duba madarar ya ga tabbas a yadda suke shan shayi wannan yau za ta ƙare, shi kuwa bai shirya siya kayan shayi yau ba, sai ya haɗawa Rauda shayi da kansa, ya zuba kaɗan haka na shi ma ya zuba rabin cokali, tana lura da shi ta ce"Sweetheart ya dai yau na ga ka zuba madara kaɗan?" Ya yi gyaran murya ya ce"Ina fa lafiya? Wannan madara da nake sha da yawa kwana biyu ita ce take tada min ulcer, to ban faɗa miki ba ne, jiya ina kasuwa ta taso min, sai da na je asibiti, na yi wa likita bayanin abubuwan da nake ji a jikina, ya ce ulcer ce ta ci ƙarfins, da tangaɗi fa ba ke asibiti jiyan nan". Rauda ta ce"Subhanallah, amma shi ne ba ka faɗa min ba?" Ya ce"Ai ba na son tada miki hankali ne, na san za ki shiga damuwa shiyasa, to likita ya ce na rage shan madara da milo sosai, sannan na rage shan suga, na daina cin doya, dankali, kaza, jan nama, ya ce duk kifi ya fi su amfani, shi ma ba sukumbiya ba, ko karfasa ko ƙawara, kin san shi karfasa ƙananu ne ba ma wata tsoka da za ki ji a jikinsa, musamman idan ya soyu, shi kuma ƙawara shi ne mai kwayoyin nan a jikinsa, amma ai ana taune su idan sun soyu, to wannan ƙayar akwai sirri a jikinta, wallahi ya ce ta fi wannan tsokar nama da muke ci, don haka dole za a canza tsarin gidan, don mu samu mu inganta lafiyarmu". Rauda ta ce"Amma ni ai ba ni da ulcer". Ya ce"To Rauda ai ba sai cuta ta kama ka mutum yake kiyaye sharuɗanta ba, kafin cutar ake ake yin riga-kafi ai, don haka ke ma ya zama dole ki kiyaye, daga yanzu kifi za a dinga ci a gidan nan, ƙawara ko karfasa". Rauda ta ce"A'a gaskiya ba zai yiwu ba Sweetheart, saboda..." Salatin da Ustaz ya rafka ne ya katse maganar da ta guntso, ya fara girgiza kai yana cewa"Subhanallah, wa iyazubillah, kaico, kaiconku ya ku matan wannan zamani masu rauni da biyewa ƙyallin duniya, kaicon macen da miji zai ce fari ta ce baƙi, kash, Rauda ban so kika kasance cikin irin waɗan nan matan ba, a ce miji yana faɗa kina musawa? Subhanallah, shin kin manta sai na ɗaga ƙafa za ki shiga aljanna? Tirr, amma kin yi min bazata, Rauda kin shammace ni". Duk sai ta ruɗe, ita ba ta ga abun rashin kunya a maganarta ba, amma sai zuzutawa yake yi, dama ta lura babu wuya ya kai mutum wuta, kamar za ta yi kuka ta ce"Ka yi haƙuri". Ustaz ya taɓe baki ya ce"A'a la ba'asa, ni kar ma ki damu, don idan ta ni ne na yafe miki, sai dai ya za ki yi da hakkin da Allah ya ratayawa mace a kan mijinta? Wannan tsakaninki da Allah ne". Ta ce"Ka yi haƙuri kuma ni ba da wata manufar na faɗa ba, me ma na ce ne da zafi? Gaskiya ka zuzuta abun". Ya ce"A haf! Rauda na yafe miki, sai kuma ki nemi yafiyar Allah". Ya tashi ya tafi ɗaki yana ɓata rai, jikinta duk sai ya yi sanyi, yau ne rana ta farko da suka fara samun saɓani da Ustaz, ta gyara falon, ta bi shi ɗaki tana ta ba shi haƙuri, yana faɗa mata shi fa ya yafe mata, kawai yana taya ta jimami ne saboda fushin da Allah zai yi da ita a kan saɓawa miji". Duk da ya yi na asuba sai ya so ya ƙara, ita kuwa ba ta jin za ta iya ba shi, don haka ta ɓata rai ta ce kanta ciwo yake yi, ya ce"A haf! Ashe dai ba za ki canza ba, ashe ba kya tsoracewa azabar Allah Rauda, shin kin san illar gujewa shimfiɗar miji kuwa?" Ta ɓata rai ta ce"Har na haddace wannan wa'azin naka, idan haddar kake buƙata yanzu zan zayyano maka ita, amma wallahi ba za ka samu komai daga wajena ba a yanzu don ni ba inji ba ce, ba kuma jaka ba ce". Ustaz Ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Ya Allah ga matata nan Rauda, mai yawan saɓawa miji, Allah na yafe mata". Ya ce"Rauda in don ta ni ne wallahi na yafe miki har zuciyata, sai dai ya za ki yi da azabar da Allah ya tanadarwa masu hali irin naki?" Ta bar ɗakin ba ta ce masa komai ba, halinsa na faɗa mata azabar Allah da tsinuwar mala'iku ya fara isarta fa, haka ya tashi ya shirya ya tafi kasuwa, wajen azhar ta kira shi a waya ta yi masa tunin kajin. Ya ce"Subhanallah, wato kenan Rauda duk irin illolin da na faɗa miki a kan cin nama da kuma muhimmancin gujewa ƙyallin duniya a musulunce ba ki yarda ba ko?" Ta ce"Na yarda mana, amma gaskiya ba zai yiwu lafiyata ƙalau na daina cin nama ba, Please ka aiko min ko ka kawo min". Ya ce"To shikenan, da yake babu cash a jikina kuma na manta ban fita da ATM ba, bari sai na ci bashin ko guda ɗaya ce, idan na dawo sai a siya ko?" Ta ce"A'a bar shi kawai bari na fita na siyo". Ya ce"Rauda bari ki fita kamar yaya? Dama haka ake fita babu izini? To kin san da cewar duk macen da ta fita babu izinin mijinta har ta je inda za ta je ta dawo duk taku ɗaya da yake yi..." Ta katse shi da faɗin"Mala'iku za su dinga tsine mata, ai na sani, kuma yanzu ba ga shi na tambaye ka ba?" Ya ce"Subhanallah! Wannan ɗaga murya da kika yi min na yafe miki, sai dai kuma ya za ki yi da faɗin Manzon Allah na cewar kar mace ta ɗaga sautinta sama da na mijinta? Anya kuwa Rauda?" Ta yi shiru, tana takaicin halin shi wani lokacin. Ya ce"Wannan labari kike ba ni to ba neman izinin fita ba, tun da ai ce min kika yi za ki fita, mata da yawa suna yin wannan kuskuren, sai dai kawai mu ce Allah Ya shirya su, Ya sa mazajensu su dinga yafe musu, sai kuma su ji da fushin Allah wanda shi ne ma babban". Ta ce"To ya ake neman izinin?" Ya ce"Alhamdulillah kin dawo kan hanya kenan, cewa za ki yi ina neman izininka zan fita na siyo kaza, ni kuma sai na ce miki na amince miki ki fita ki siyo kaza cikin aminci ki dawo cikin aminci, to wannan shi ne asalin neman izini, gwada mu gani". Ta ce"Ina neman izininka zan fita na siyo kaza" Ya ce"Alhamdulillah, Rauda matata na amince miki ki fita ki siyo kaza cikin aminci, ki dawo cikin aminci". Ta sauke numfashi ta ce"Na gode" Ta katse wayar a ranta tana ayyana iyayin shi ya yi yawa. Ta ɗauki ATM ta fita, ta siyo kaji guda biyar, dankali da doya har da kayan shayin, ta duba duk wani abu da take buƙata ma ta ƙara siya, har lemula ta siya wanda za a ƙara a firji, mai adaidaitasahun ya kawo ta har kofar gida, ta dinga shiga da kayan, da Ustaz ya dawo ya gani ya yi ta farinciki, a ransa ya ce 'Ashe ma kina da kuɗin da kika noƙe'. Tun da ya dawo gidan yake haɗiyar yawu, saboda sai a lokacin take yin pepper soup ɗin, yana so ya ci ga shi babu dama, ta gama ta shiga ɗaki za ta yi wanka, ya lallaɓa ya ɗauki guda ɗaya ya fita tsakar gida ya ci ya tauna ƙashin, sannan ya dawo falon, haka ta cinye tass a gabansa ko tayi ba ta yi masa ba, sai da ta je ta kwanta ya shiga kitchen ɗin ya lashe romon ya cinye ƙashin, a ransa yana faɗin Allah Ya isa, na cuci kaina Allah Ya ba ni ikon jurewa. Da safe ma haka ya sha shayi da madara kaɗan, ita kuwa sabon gwangwanin ta buɗe ta zuba don ranta, takaici ya ishi Ustaz, sai da ta koma ɗaki shi kuma ya shiga kitchen ɗin don yin wanke-wanke ya haɗa wani shayin ya zuba kayan shayi wadatattu ya shanye, daga ranar kuma yake yin haka. Aurensu yana yin wata ɗaya Babanta ya kira shi, ya faɗa masa ya sama masa gurbi a wani shagonsa, na siyar da kayan electronics, don haka idan ya shirya sai ya fara zuwa, Ustaz ya kamu da farinciki ya ce a shirye yake, ya dinga jero godiya, Abba ya ce"Babu komai Malam ai yi wa kai ne wannan, fatana dai ka kasance mai riƙe amana, idan na samu yadda nake so daga gare ka in sha Allah gaba zan ɗora ka a harkar shigo mana da kaya daga waje na zaman shago ba". Ustaz ya dinga godiya daɗi kamar ya kashe shi, har ya fara hango shi ya zama babban attajiri, ai shirinsa na farko shi ne ƙara aure, don biyun sai ta fi daɗi Yayinda ake yi wa Ustaz wannan albishir ita kuma Rauda tana zaune a falo suna waya da ƙawarta Zainab, faɗa mata take yi ita fa har yanzu an yi wata da auren nan lamarin babu canji, ta gaji ba za ta iya jurewa ba. Zainab ta ce"Ko dai ke raguwa ce Rauda? Ni wallahi da zan samu ma mijina ya dawo kamar haka da na ji daɗi". Rauda ta ce"Ba za ki gane ba ne Zee, ni dai gaskiya na gaji, dama fa sai da ya faɗa min shi hariji ne, ni ai ban san haka harijin yake ba, gabaɗaya na daina sha'awar sex ɗin ma". Zainab ta miƙe tsaye kamar Rauda tana kallonta ta ce"Hariji? Da gaske? Wai kina nufin ba minti biyar take yi ba zuwa goma?" Rauda ta ce"Haba Zainab idan minti goma ne har kya ji kanmu? ko ashirin ma ai zan jure, sai ga na ture shi kawai, idan don ta shi ne ya kwana yana yi fa, wajen nan kullum sai na yi masa gashi sau uku ina dalili?" Zainab ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Rauda kina cikin masifa da bala'i, kin san wane ne hariji kuwa?" Gaban Rauda ya ba da rass, ta ce"Kamar ya bala'i?" Zainab ta ce"To ai gara ma bala'i ke duk wani jafa'in duniyar nan kawai ma ki ce kina ciki, kin san kuwa akwai ƙanwata wacce muke 'yar wa da 'yar ƙani yanzu haka ta haukace silar auren hariji? To wata ƙawar maƙociyata ita ƙarshe ma mutuwa ta yi, mai kuɗi ne ta aure shi, ashe hariji ne, ya tisa ta a gaba, ta gudu gida iyayenta suka kora ta, ke abu yana gaba matar nan har ya kusa haɗe mata gabanta da bayanta, abu ya zama kamar ƙofar gari amma duk da haka bai saurara mata ba, wani dare yana cikin yin abun ya ji ta daina numfashi, sai da ya gama abunsa ya lura ta mutu". Rauda ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". Zainab ta ce"Ai Innalillahi tukunna ma, wallahi duk wacce ta auri Hariji kuma ta ce dole sai ta zauna da shi to fa ɗayn biyu ne zai faru, ko dai ya kashe ta, ko kuma ya mayar da ita harija ita ma abun ya daina isarta, kuma wallahi yawanci ƙarshe mutuwa ake yi, mutuwa za ki yi saboda kullum cikin huƙatar abun kike, idan kuma ya riga ki mutuwa ki kasa zaman aure, duk wanda kika aura ya gan ki a haka sakinki zai yi, don ba zai yarda ki kashe shi ba". Rauda ta shiga tashin hankali, ta ce"Na shiga Zainab ya zan yi?" Ta ce"Tabbas kin shiga uku wallahi, kuma kin yi kuskuren zama da shi har wata ɗaya, har ma mutum ya ce miki shi hariji ne kuma ki yarda ki aure shi? Lallai kin yi ganganci, Allah Ya ji ƙanki". Rauda ta ce"Yanzu mene ne abun yi ya zan yi?" Zainab ta ce"Tattara kayanki za ki yi ki tafi gidanmu ko sanar da su halin da ake ciki, idan kuma kin ga za ki iya ga wajen nan, sai mu ce Allah Ya kyauta makwanci". Rauda ta ce"Amma fa ina son shi". Zainab ta ce"A haf, To wallahi ya mayar da ke harija, kin ga sai anjima". Ta katse kiran. Rauda ta zauna ta fara hawaye tana auna maganganun Zainab, tabbas da wannan abun sai a kashe mace wallahi, kenan ana nufin a haka za a rayu dama ba zai rage ba? Ai kuwa da sake, tana son shi amma hakan ba zai sa ta bari ya lahantata ba, don haka ta murɗa key a ƙofar kafin ya dawo. 08028966015 [31/10, 5:26 pm] Sadiya Abdulrazak: 32 Ustaz ya dawo gida da farincin samun aiki, dayake da mukullinsa yake buɗe gidan, ya buɗe ya shiga, ya shiga ɗakin da sallamar shi, ya yi zaton har ta yi bacci, don haka ya rufe ko'ina ya kashe kayan kallo yana mita da faɗin"Allah Ya haɗa ni da shagalalliya, ba za ta daina kallon nanaye ba, kaico". Ya nufi ɗakin nasu, ya tura ƙofar ya ji ta a rufe, ya fara ƙwanƙwasawa yana mamaki, Rauda ta yi banza da shi, ya leƙa ta windo ya hango ta a kan gadon ta juya baya kamar mai bacci, ya fara kiranta "Rauda, Rauda". Ta yi banza da shi, kiran duniyar nan ta ƙi ko motsi, abun ya na shi mamaki don ya san tana ji, tun da a jikin window ya tsaya, kuka gadon babu nisa da windon, ya yi ƙwafa ransa duk ya ɓaci ya nufi kitchen, ya zuba abinci ya ci har da haɗa shayi, ya ɗan zauna a falon a ƙoƙarinsa na nuna mata fushinsa, ya yi zaton za ta zo ta buɗe ta nemi ya shigo ɗakin, idan ma wasa take yi masa ya yi mata bayanin miji ba abun wasa ba ne, ba ya son irin wannan wasan, sai ya ji shiru har goma ta wuce, ga shi lamarin jikinsa ya fara kankama taimakonta kawai yake buƙata, a dole ya tashi ya koma ɗakin ya cigaba da kiranta, ƙarshe ya kira wayarta, ta dinga ringing tana kusa da ita amma ta ƙi ɗauka, ya rasa abin da yake yi masa daɗi, dabara ta faɗo masa ya ɗakko ruwa pure water ya ɓula ledar, ya zura ta windon saitin da take kwance ya fara jiƙata, ta tashi zauna tana ɓata rai ta ce"Malam lafiya mene ne haka?" Ya hangame baki da mamaki ya ce"Rauda, shin kin makance ne ko magagin bacci ne bai sake ki ba? Bi ma'ana ba a hayyacinki kike ba?Ban gane lafiya ba, ai ke zan tambaya lafiya?" Ta ce"Wallahi ba zan sake kwana ɗaki ɗaya da kai ba, don haka ka koma inda ka fito, don wallahi ba za ka kashe min rayuwa ba kwanana bai ƙare ba". Ustaz ya ji wani tashin hankali ya ruguzo masa, ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Raudatu me kike nufi, yi min da larabci ko zan fi ganewa, bi ma'ana ban gane wannan yaren da kika yi min ba". Ta ce"Kar Allah Ya sa ka gane". Ya ce"Subhanallah, Ya Allah ka shaida na yafewa matata Rauda, sai dai ya za ta yi da hakkina da take shirin ɗauka?". Ya cigaba da buga ƙofar ya ce"Rauda buɗe mu yi magana ko za mu fahimci juna, babu kyau haramun ne ka dinga hora mutum da laifin da bai san ya yi ba, ki yi mini bayani me na yi miki?" Ta ce"Kai hariji ne, kuma cutata kake yi, nema kake ma ka kashe ni, don haka ba zan iya ba, ba zan iya zama da hariji ba, a san abun yi kawai". Ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Hana Rauda, idan kika yi min haka ba ki yi min adalci ba wallahi". Ta kwanta ta juya masa baya, ya dafe kai kamar zai kurma ihu don takaici, ya ce"Raudata yi haƙuri daure kin ji ki buɗe min, in sha Allah za mu fahimci juna, idan kin gaji ne sai a duba a yi minus, a rage tun da dai ba zai yiwu a daina gabaɗaya ba ko?" Ta yi banza da shi, ya ce"To Rauda a matsayina na mijinki ina nemanki, bi ma'ana ina buƙatar ki ba ni hakkina na aure, bi ma'ana a raya sunna, kuma kin san hukuncin macen da mijinta ya neme ta ta ƙi ba shi haɗin kai, idan na yafe miki ya za ki yi da tsinuwar mala'iku?" Rauda dai ko motsi ba ta sake yi ba, ya dinga yi, ya yi wa'azi ya yi magiya, har bacci ya ɗauke ta da gaske, shi kuma ya gaji da tsayuwa, a dole ya koma wani ɗakin ya kwanta, sai dai ya kasa bacci sai da ya yi istimna'i, ga kuma fargaba da ta addabe shi, yanzu idan Rauda ma ta guje shi anya kuwa zai sake auruwa? Kuma babban tashin hankalinsa yanzu idan ta gudu ya matsayin aikinsa da babanta ya ba shi? Kar fa ya ƙwace abunsa, ai kuwa da sake, dole ya lallaɓata a yi minus, idan ya so ta dinga na shi na daren ma kawai ya haƙura, don ya sha wahalar zaman gwauranci bayan ya rabu da Sayyada, ba zai so ya maimaita ba. Haka ya kwana a wahale, washegari da safe ya gyara gida ya dafa shayi, ya soya dankali, ya ci rabi ya goge bakinsa, ya ajiye mata rabi, zama ya yi a falon, ba shi da shirin zuwa kasuwa, don ya ma daina zuwa, sai dai ya je ya yi musu sallama kawai, Rauda tana ta jira ta ji fitarsa ta fito, amma ta shi shiru, sai da ta fara jin yunwa ta daure ta fito tana ta ɓata rai. Kallonta kawai ya yi wani yawu ya tsinke ya silala maƙoshinsa, saboda jiya ya kwana da kewarta ba kaɗan ba, ya ce"Sannu da fitowa, kin tashi lafiya?" Ta ce"Lafiya lau". Ta wuce kitchen, ya tashi ya bi ta, yana ƙarasawa ya rungume ta ta baya, ta ce"Don Allah sake ni". Ya ce"Wannan matata ce kuwa? Gaskiya masoyiyata Rauda ba za ta yi mini haka cikin hayyacinta ba, me na yi miki don Allah, ki faɗa min na gyara kuskurena". Ta ce"Ba kuskure ba ne, ba kuma laifinka ba ne, kawai kasancewarka hariji ya sa na gane ba mu dace da juna ba, kamata ya yi ka nemi harija ni kuma na nemi mai lafiya, don cigaba da zamanmu akwai cutarwa". Ta fizge ta fara ƙoƙarin kunna gas, ya ja baya yana cewa"Ga abincin can fa a dining na yi miki dankali da shayi, kuma akwai biredi ma". Ta fita ba ta kula shi ba, ya bi bayanta, ya riga ta ƙarasawa ya haɗa mata shayin, ya zuba mata dankalin a faranti ya tura gabanta, ya zauna ya ce"Ko na ba ki a baki?" Sai ta ji tausayin shi kaɗan, Allah Ya sani tana son Malam Ashir, kuma kyautatawar da yake yi mata da haƙurinsa ta san ba duk wani namiji ne zai yi ba, yanzu jiya duk abin da ta yi masa amma yau ya tashi ya mata girki bai fasa ba, har ma yana so ta ba shi dama ya ba ta a baki, yana da kyakkyawar zuciya, amma hakan ba zai sa ta zauna ya kashe ta ba ko ya nakasa ta. Ya ce"Me na yi miki don Allah, indai wannan ne za a yi minus one, yanzu zan dinga haƙuri idan za ki ba ni sau ɗaya kullum, kin ga sai ya zama da daddare kawai za a dinga yi ko?" Ta ce"Ni fa ba zan iya ba, ai ko sau ɗayan ma cutata za ka yi, tun da mutane normal ba haka suke yi ba, an ce min na a fin awa ɗaya ko minti talatin". Ustaz ya ce"Subhanallah! Allah Ya yi min tsari da minti talatin, Rauda kin san wane ne mai irin larurata kuwa? Jina nake ko kwana uku zan yi ban guda daga gare ki ba ba zan gamsu ba, ana bari kawai don ba shi aka turo mu duniya ba, a yi dai zancen da zai yiwu, amma maganar minti talatin ko awa ɗaya ba ta taso ba, me aka yi da maza?" Ta ce"To ai shikenan, ka sake ni ka auri wacce za ta iya kawai". Ya ce"A haba wannan ai zance ne, Rauda ni da ke mutu-ka-raba in sha Allah". Ta ce"Wallahi ba zan iya ba, zan sanarwa iyayena tun wuri su san halin da nake ciki". Ustaz ya ce"A'a Rauda don Allah kar ki zama matan da suke bankaɗa sirrin shimfiɗar aurensu, idan na yafe miki ya za ki yi da hukuncin da Allah Ya tanadawa waɗan nan mata? Ina son rayuwa da ke har aljanna, don Allah ki riƙe min sirrina, kar ki zama Sayyada da Maraƙisiyya". Ba ta sake magana ba, ta gama karyawa ta tashi ta tafi ɗaki, ya tattare wajen, ya bi ta, ya tarar ta rufe ƙofa, ya ce"Innalillahi wa ilaihi raji'un, ashe dai wahala ba ta ƙare min ba ni Ashir". Ya koma falo ya zauna yana ta tasbihi, tunanin Sayyada ya faɗo masa, ita tana jin wa'azi ta amince ko ba ta so, amma wannan kamar 'yar Fir'auna? Sannan ba zai iya yi mata ta ƙarfi ba kamar yadda ya sha yi wa Maraƙisiyya, ita wannan lallaɓa ta zai yi tun da ya ga aurenta zai zame masa jari, ga shi daga aure wata ɗaya ya samu canjin wajen aiki, dole zai haƙura da wasu abubuwan su yi komai cikin lumana da sasanci. Ta ɗauki waya ta ba wa Zainab labarin abin da yake faruwa ta whatsApp, ba ta online ma, ta kira ta ta faɗa mata ta yi mata magana ta hau online, ai kuwa tana hawa ta saurara ta yi mata voice ta zuge ta tass, ta ce"Wallahi ke ma Rauda son shi kike, na lura ba kya tsoron mutuwa, indai kina zauna a gidan ai wallahi sai ya yi miki kwanta-kwanta ya haike miki, ko lafiyayyen miji ne kuka kwana biyu ba kwa tare ranar da kuka haɗu ya take kasancewa? Ballantana kuma hariji, Rauda Allah Ya ji ƙanki kawai". Rauda ta rikice ta ce"Don Allah ki daina tsorata ni, ki faɗa min ya zan yi?" Ta ce"Ki tattara kayanki ki bar gidan, ki je gida ki faɗi halin da ake ciki, Wallahi idan ba haka ba za ki tsinci talatarki a Laraba". Rauda ta ce"To bari na tafi". Ta tashi ta hau haɗa kayanta, kuma a cikin zuciyarta ba ta som tafiyar, tana son shi, sannan ba ta so a ce aurenta zai mutu a yanzu ba, tana ma jin kunyar bayanin da za ta yi idan ta je gida, haka ta fito tana jan akwati, Ustaz yana kwance yana karatun Qur'ani a wayarsa ya ga fitowarta tana jan akwati, ya kai aya ya ajiye wayar, ya tashi da sauri ya nufe ta hankali tashe, ya ce"Rauda, Raudata me zan gani haka?" Ta ce"Gidanmu zan tafi, ai na faɗa maka ba zan iya ba". Ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Haba Rauda me ya yi zafi? Mene ne damuwar wai? Kin ga zauna don Allah, ki rufa min asiri na ga samu kuma na ga rashi?" Ya ce"Ba abin da za ka faɗa min na yarda da kai, don haka ka ba ni hanya". Ya zube a gabanta ya fashe da kuka amma babu hawaye ya ce"Don darajar Allah da Manzonsa ki yafe min Rauda, soyayya ce ta haɗa mu ba ƙiyayya ba, ba dai a kan raya sunna ba ne? To daga yau na yarda a rabu da arnan nan su yi ta rayuwarsu, ba sai an kashe su ba, sai dai kuma su arna suna iya yaɗa ɓarna a bayan ƙasa, dama shi ne amfanin auren don a kashe su a kauda ita ɓarnar, amma tun da kin ce haka ni na haƙura wallahi, na yi miki alƙawarin ba zan sake nemanki ba, sai dai idan kin ji marmarina sai ki faɗa min, kina da dama tun da ai hakkinki ne ko?" Jikinta ya yi sanyi, kuma ta ji tausayin shi, kuma ta ji a ranta indai da gaske yake za su rayu a haka ba zai neme ta ba za ta haƙura su zauna, ta ce"Ka yi alƙawarin da gaske ba za ka sake nema na ba?" Ya ce"Ƙwarai kuwa, in sha Allah ko gado ɗaya muka kwana sai dai mu kalli juna, zan daure in sha Allah, ai kowane bawa da kalar ƙaddarar shi, amma don Allah ki dinga yi min adalci" Ya ƙarasa maganar muryarsa tana rawa. Ta ce"To na ji, amma daga ranar da ka saɓa alƙawari zan tafi gidanmu". Ya ce"In sha Allah ma ba zan saɓa ba". Ya karɓe akwatin ya mayar ɗakin, ya buɗe ya jera kayan duka a sif ɗin, tana zauna a gefen gado tana kallon shi, ya gama zai fita ya kalle ta ya ce"To shikenan Rauda Allah Ya ba ni ikon jurewa, kuma ni fa na yafe miki". Ya fita daga ɗakin, ta bi shi da kallon tausayi, ta ɗauki waya ta faɗawa Zainab yadda suka yi da shi, Zainab ta ce mata wannan fa ba dabara ba ce, saboda ba lallai abun ya ɗore ba, Rauda ta ce ta ga alamar zai ɗore, saboda ta ga nadama a fuskar shi. Suka wuni a falo suna fira kamar komai bai faru ba, suka yi girki tare suka ci abinci, da yamma ya fita ya je kasuwa ya sanar da su zai fara wani aikin, bai dawo ba sai dare, bayan ya ci abinci yake tambayarta"To Rauda ya batun makwanci fa? Za mu raba ne ko kuma a ɗaki ɗaya za mu cigaba da kwana?" Ta ɗan yi jim kafin ta ce"Ba matsala za mu iya kwana tare, kai dai ai ka san alƙawarin da ka yi ko, sai ka yi ƙoƙarin kiyayewa". Ya ce"In sha Allah zan kiyaye". Da aka zo kwanciya sai ta saka filo guda biyu a tsakaninsu, ta kuma juya masa baya, Ustaz ya rasa ta ina zai fara wannan sabuwar rayuwa mai cike da sammatsi. Haka suka kwana ya daure bai ko gwada taɓa ta ba, amma yana ji a jikinsa fa. Haka aka fara sabon zama, Ustaz yana ta ƙoƙarin daurewa, ita kuma ko a jikinta, kuma haka za ta dinga shiga ta ɗaukar hankali, sai dai ya kalla ya haɗiyi yawu. Cikin satin ya fara zuwa aiki, shago ne babba wanda ake siyar da electronics, aka fara nunawa Ustaz yadda kasuwar take, kuma yana fahimta, yana gudanar da komai cike da ɗaukin abun. Tun yana daurewa har abun ya fara fin ƙarfin shi, sai ya tsiri wani abu, sai Rauda ta yi bacci sai ya tashi ya kunna fitilar wayarsa ya dinga haskata, yana kallonta yana haɗiyar yawu, kuma hakan ƙara masa wahala kawai yake yi, idan ya kunnu da yawa sai ya bar ɗakin ya koma falo ya biyawa kansa buƙata. Watarana yana falo yana yi, Rauda ta farka yin fitsari, ta ga ba ta gan shi ba, ta leƙa falo ta gan shi ya hau kan hannun kujera yana ta motsa jikinsa, gabanta ya faɗi, don idan ba ka kalle shi sosai ba sai ka ce da mace yake tare, yadda duk ya fita daga hayyacinsa, ta koma ɗakin, ta zauna a bakin gado, tausayin shi sai ya kama ta, ta fara tunanin anya Allah ba zai kamata da hakkin mijinta ba kuwa? Kuma ita ma fa tana jin kewar shi a wasu lukotan, amma inda a ce zai tsaya a iya romance, abin da ta yi kewa kenan ba wancen babban lamarin ba, ta koma ta kwanta jiki a mace, tana tunanin za ta faɗa masa su yi yarjejeniya idan zai dinga romance ɗin. SAYYADA A lissafina cikina watansa uku ya shiga na huɗu, amma na fara jin motsin shi kaɗan-kaɗan, ina nan ina ta lissafin watannin haihuwata, Mama har yanzu ba ta gama sakin jiki da ni ba, 'yar firar nan mun daina, Baba dai yana kula da ni sosai, zan iya cewa ba ni da damuwa sai ta zuciyata, soyayyar Sadam ce take ragargaza ta, wani lokacin idan na matsa kaina da tunanin shi fitar numfashina har canzawa yake, wani irin son shi nake ji wanda ban ji ba ko a farkon haɗuwarmu, ga shi ba ni da damar da zan bayyana masa, ina cikin idda, sannan ba a ba ni wayata ba har yanzu, kuma uwa-uba na san yana can yana fushi da ni, ƙila ma da gaske yake ya haƙura da soyayyata, idan na tuna yana can tare da matarsa sai baƙinciki ya turnuƙe ni, na matsu na fara zuwa awo ko Allah zai sa watarana mu haɗu idan ya kawo shaguɗaɗɗiyar matarsa, wancen satin na ce da Mama zan fara zuwa awo ta ce nmin ba yanzu ba, na lura sam ba ta son abin da zai saka na fita waje, kuma ban ga laifinta ba, tun da ni ce na saka mata zargina. 08028966015 [01/11, 8:22 pm] Sadiya Abdulrazak: 33 Ustaz ya kwantar da kai sosai a wajen Rauda, sam bai taɓa gwada nemanta ba, sanda ta zo masa da batun a dinga romance ya ce ba ya so saboda abun akwai sammatsi, zai iya kasa riƙe kan shi, tana jin tausayin shi, amma Zainab tana ƙara zuga ta kan illolin zama da hariji, a haka suka dinga zaman, sai dai yana yawan kunna wa'azin da ke nuni da hakkin miji a kan matarsa ko ya kunna wanda ake gargaɗin mata masu ƙauracewa miji, amma ba ya ma nuna don ita ya kunna. A ɓangaren kasuwanci kuma Alhamdulillah yanzu ya san makamar aikin, kuma mahaifin Rauda ya yi masa duk wasu gwaje-gwaje ya yarda yana da amana, sam ba ya cogen kuɗi, tun da ya sha gwada shi, ya yi kamar ya manta lissafin, amma sai Ustaz ya tuna masa s ji kuɗin daidai ko naira biyar bai rage ba, wannan abu ya farantawa mahaifin Rauda, don haka ya saka shi a babban shagon shi, ya ba shi matsayin babba a shagon, da kuma alƙawarin zai dinga aikensa ƙasashen waje ya dinga siyo kaya. Alhamdulillah Ustaz harka ta buɗe, yana samun kuɗi, amma wannan mammaƙon na shi yana nan, sai Rauda ta ɓata rai sosai sannan yake yin cefanen arziƙi, kuma har yanzu yana nan a kan bakanshi ba ya cin nama, sai dai ya faki idonta ya sata ya ci. A hankali Rauda ta fara jin hukuncin da ta yanke ya yi tsauri, da gaske kewar mijinta take yi, kuma tana jin kunyar faɗa masa, tun tana daurewa har dai wani dare ta neme shi, Ustaz kuwa ya ce da wa Allah Ya haɗa ni? Ya gwangwaje sosai, ta samu gamsuwa, duk da ta wahala, tun daga wannan ranar sai Rauda ta zama kamar ita ce mijin Ustaz matar, sai ranar da ta bushi iskanta sai ta neme shi, shi kuma babu zuciya sai ya amsa kira, yana jin zafin lamarin zaman nasu sosai, amma yana daurewa ne saboda alkhairin da ya samu ta silarta, kuma duk shirinsa shi ne sai ya gama kafuwa ya zama mai kuɗi sannan zai gallo mata kishiyoyi, don mata biyu yake burin ya aura a rana ɗaya, idan ta ga dama ta zauna sai su zama su uku, ya dinga rabon kwana kwana ɗaiɗai, duk tsiya dai duk ragwantarsu ai idan suna hutun kwana biyu ba za su dinga yi masa raki ba, da wannan tunanin yake haƙuri da tsarin Rauda. To sai ga shi ma a hankali ita ma Rauda ta zama 'yar gari, tun da yanzu neman nashi fashin kwana ɗaiɗai take yi, idan ta neme shi yau gobe sai ta huta, ana haka ne kuma ta samu ciki, da fari ta yi laulayi, amma yana yin wata huɗu ta daina laulayi, sai kuma take jin yawan sha'awa, don haka kusan kullum yanzu sai ta nemi Ustaz, shi kuwa farinciki kamar ya kashe shi, har wata 'yar ƙiba ya fara yi. SAYYADA Duk yadda Mama ba ta so na fita dole sai da na fitan da lokaci ya yi, cikina yana cika wata biyar Baba ya ce ya kamata na fara zuwa awo, na ce to, ranar Alhamis ne aka yi maganar, ai kuwa har zumuɗin zuwan ranar Litinin nake, fatana ɗaya idan na je asibitin na haɗu da Sadam ko a hanya ne, na faɗa masa ba yaudarar shi na yi ba, a ƙalla ya daina fushi da ni ko da zai daina sona, duk yadda zan yi na ga na cire son shi daga zuciyata na kasa. Ranar Lahadi da daddare muna zaune Baba yana cin abinci yake ce min"Gobe da wuri za ki tafi asibitin? Kuma nawa ne zai ishe ki?" Na ce"E da wuri ake zuwa, kuɗin kuma ka bar shi ina da kuɗi". Ya ce"Kika samu a ina?" Na ce"Dama tuna account ɗina tun ina gidan Sadam". Ya ce"Ok, amma duk da haka zan ba ki ɗin, hakkin mijinki ne ya ba ki, ni kuma na ɗauki alƙawarin idan ba abun ya gagare ni ba ne ba zan tambaye shi ba, musamman ma da ni ne na dakatar da shi, don haka ki adana kuɗinki, ga nawa ki yi amfani da shi". Ya yi maganar yana miƙo min kuɗi, na karɓa na ce"An gode Baba Allah Ya ƙara arziƙi". Mama ta ce"Goben tare za mu je ma ai". Baba ya ce"A kan me? Sayyadar ƙaramar yarinya ce da sai kin raka ta wajen awo?" Mama ta ce"Shikenan". Ya ce"Ko akwai wani dalilin da yasa kike son rakiyar?" Ta ce"Babu komai, shikanan Allah Ya kai ta lafiya". Na tashi sum-sum na bar wajen, na san dai Mama zargina take shiyasa har ba ta yarda na tafi asibiti ni kaɗai ba, jikiwnsa duk ya yi sanyi, na ƙirga kuɗin dubu goma ne, na adana na nemi waje na zauna, Baba yana fita daga gidan Mama ta shigo ɗakina, sai da gabana ya faɗi da ganinta, tun da na san ba ni da cikakkiyar gaskiya, ta zauna ta ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ta ce"A zahiri za ki fara zuwa awo ke kaɗai, amma a baɗini ba ke kaɗai ba ce za ki fara zuwa, akwai Allah, yana kallonki yana jinki, dokarsa kike burin takawa, ki sani idan kin cigaba da soyayya da wanda kika so da aurenki to dokar Allah kike takawa ba tawa ba, kuma za ki iske shi a madakata ki karɓi hukuncinki, ki ji tsoron Allah Sayyada, ko me za ki yi ki haƙura ki kallama iddarki, kuma kar ki manta na rantse ke da auren Saddam sai dai a lahira, idan kika sake kula shi kuma Allah Ya isa ban yafe miki ba". Hawaye ya zubo min na kasa cewa komai har ta ban ɗakin, wannan kalmar ta cewar ni da Sadam har abada tana firgita ni, ji nake kamar suna cewa na yi sallama da farinciki ne a rayuwata, don shi ne farincikina, haka na kwana da tunani barkatai. Washegari da sassafe na tashi na shirya, na sha kunun da Mama ta dama na tafi awo, tun da na fita daga gida nake jin daɗi saboda na sabunta iskar da nake shaƙa, ina ta takawa a cikin layi har bakin titi, riga da zani na saka na atamfa da hijjabina har ƙasa, yau ban saka niƙabi ba, na tari adaidaitasahu na hau muka kama hanyar asibitin, a raina ina fatan na ga Saddam, amma idan na tuna Allah Ya isa da Mama ta yi min sai jikina ta yi sanyi, na ji ko na gan shi ba zan iya yi masa magana ba, haka na shiga asibitin ina ta kalle-kalle, karaf idona ya sauka a kan motar shi, na ƙare mata kallo tabbas ita ce, nan take bugun zuciyata ya canza, na daburce na rasa ma me ya kamata na yi, wata zuciyar tana faɗa min na je na fahimtar da shi yadda abun ya kasance a ranar da ya ban maganin nan, wata zuciyar tana faɗa min shi ma fa bai damu da ni ba, ya daina so na, ga kuma kalaman Mama na maimaita kansu a cikin kaina kamar yanzu take furtawa, amma haka Shaidan ya yi min linzami ya tallafi ƙafafuna na fara takawa a hankali har na isa wajen motar, akwai tint a gilashin don haka ba zai yiwu na ga na cikin motar ba, jikina ya fara ba ni yana ciki yana kallona, don haka na ƙwanƙwasa, shiru ba a buɗe ba, na ɗan yi kamar minti biyu a tsaye, na shagwaɓe fuska wai ko zan ja hankalinsa ya buɗe amma shiru, har na gaji na bar wajen ina waiwayen motar. Hankalina duk ba a kwance ba har aka gama yi min awo, tun ƙarfe takwas nake asibitin dai sha ɗaya na gama, na yi mamakin ganin har yanzu motar tana wajen, na sake zuwa na ƙwanƙwasa shiru ba a buɗe ba, sai na yi tunanin ko ya ajiye motar ne ya tafi wani wajen, na nemi waje na zauna a gefe da ƙudurin ko zan kai magriba sai na jira dawowar shi, ban can wajen sha biyu da mintuna sai ga wata mace ta zo ta tunkari motar, gabana ya faɗi da na gane kenan jiranta ya zauna yi shi yasa ya ƙi buɗe mini? Na tashi bisa shawarar zuciyata na ƙarasa wajen motar, daidai lokacin da ta shiga mazaunin direba ta zauna, zuciya ta raya min matarsa ce, duk da ban santa ba, ban kuma tabbatar ba, na ce"Safna". Ta juyo ta kalle ni, nan take ta haɗe rai sosai, ta fito daga motar ta ce"Lafiya? Bashi ko tara?" Na ce"Babu ɗaya". Na juya zan tafi, ta janyo hijjabina na dawo baya, ta ce"Uban me ya kawo ki asibitin nan, bibiyata kike yi?" Na yi dauriya matuƙa ban sharara mata mari ba, na fizge hijjabina na ce"Ke ba ki kai wacce zan bibiye ki ba". Ta yi dariyar rainin hankali ta ce"Amma mijina wanda yake bibiyata ya kai ko?" Ban ce komai ba na bar wajen da sauri, ina ji tana ta zagina ko juyowa ban yi ba, zuciyata sai zafi take yi min, wani kishin da ya taso min ganga-ganga, kenan dai idan na fahimta ya bar mata motarsa ne? Ashe ni ce nake ta haukana shi yana can yana farantawa matarsa, na share hawaye da suka sakko min, na fita daga asibitin na hau adaidaitasahun na koma gida, na ci sa'a Mama ba ta yi min magana a kan daɗewata ba, ranar haka na wuni kamar mara laka, kawai na saddaƙar ni kaɗai nake son Sadam, shi matarsa yake so, a fili na furta "Allah ka yi min zaɓin alkhairi ka cire min ƙaunar wannan bawa naka mara adalci". Tun daga ranar nake ƙoƙarin mantawa da shi, amma na kasa, dabara ɗaya na samu idan na fara tunanin shi sai na ɗakko Qur'ani na fara karatu, kuma Alhamdulillah ina samun samun sassauci sosai. Ranar da zan koma asibiti haka na dinga fargaba da fatan Allah Ya sa kar na haɗu da Safna, a dole na saka niƙabi, kuma Allah Ya karɓi addu'ata ban ganta ba, amma na ga motar Sadam ɗin. Haka rayuwa ta cigaba da miƙawa, cikina yana ƙara girma, har na shiga watan haihuwata, ina ta lissafin EDD ɗina, da Mama ta sanarwa Baba na shiga watan haihuwata, sai ya kira Ustaz a waya ya faɗa masa, Ustaz ya ce"Alhamdulillah, ma sha Allah, Allah Ya raba su lafiya, to Baba idan ta fara naƙuda sai a yi gaggawar sanar min, saboda na zo a yi komai a gabana, bi ma'ana shi yaron ko yarinyar idan an haifa kafin wasu mintoci akwai addu'a da nake so na fara yi masa, kafin ma a kai ga huɗuba, sannan me ake buƙata na kawo kafin haihuwa" Baba ya ce"Ba a buƙatar komai, na faɗa maka ne don kana da hakkin sani, ban sani ba ko za ka tanadi kuɗin hakika da sauransu". Ustaz ya ce"Za a samu in sha Allah, ai Baba yanzu Alhamdulillah ana samu daidai gwargwado, sai dai kuma ita Sayyada lambarta ba ta shiga idan an kira ta, ko za ka faɗa mata ina son magana da ita?" Baba ya ce"Me kake so ka faɗa mata?" Ya ce"Dama wai ina so mu yi shawara ne na kayan Baby da ale siya kafin haihuwa idan kuma kuɗin zan bayar sai na bayar". Baba ya ce"Ba dole sai kun tattauna ba, ka yi komai iya ƙarfinka". Ustaz ya ce"La ba'asa, a huta lafiya Baba". Suka yi sallama, na sauke numfashi, na ji daɗi da Baba ya hana ya yi magana da ni, saboda ba zan ma iya ba, tsakani da Allah na tsani Ustaz ba kaɗan ba, har yanzu ina jin zafin shi. Kwana biyu da yin wayar nan da shi, sai ga mahaifiyarsa da yayarsa sun zo gidanmu, aka gaisa a mutunce, suka ba da leda mai ɗauke da kayan Baby, duk kayan da za a buƙata kafin dai a san mace za a haifa ko namiji, muka yi godiya suka tafi suna Allah Ya raba lafiya. Cikina ya yi nauyi sosai, har na wuce EDD ɗina da kwana uku, ƙafafuna duk sun kumbura, duk yadda Mama ba ta so na fita amma yanzu ita take cewa na dinga fita ko da daddare ne ina zagayawa, amma sam ba na iyawa, kunya nake ji a gan ni da ƙaton ciki, amma a cikin gida kam ina shan zirga-zirga, da safe idan na karya na gama gyara gida ba na zama, na yi ta zagaye kenan daga farkon gidan zuwa ƙarshen shi, na kai na dawo har sai na ji na gaji, sai na zauna na huta, na cigaba, haka zan ta yi har sai lokacin girkin rana ya yi sai na taya Mama, idan na ci na yi wanka na yi sallah na yi bacci, bayan la'asar zan cigaba har sai magriba ta kawo kai, sannan da daddare a ɗakina ma ba na zama zan ta yi har sai na fara jin bacci. Wata rana na je awo na gama komai na fito na haɗu da Sadam a bakin ƙofar asibitin yana shirin shigowa, da alama shi ma bai tsammaci gani na ba, don na ga ya yi turus ya dakata da takun kamar yadda na dakata, muka shiga kallon kallo, zuciya ta raya min yanzu fa matarsa ya biyo saboda tsabar so, nan take haushi da kishi suka turnuƙe ni, na fizgi sagaggun ƙafafuna na fara jansu sharf-sharaf zuciyata na zafi, na yi zaton zai biyo ni mu tattauna, amma da na juyo sai na ga har ya shige, na sake jin wani rauni ya rufto min, da gaske Sadam ba ya sona, ina adaidaitasahu ina share ƙwalla, ina komawa gida kuma na fara jin alamun naƙuda, zuwa azhar ciwon ya fara kankama, Mama ta kira Baba ta faɗa masa, ya dawo gida muka tafi asibiti, sai bayan magriba na haifi ɗana namiji mai kama da baban shi, ina kallon fuskarsa a raina na ce'Allah Ya da kar ka yi halin mahaifinka'. Ina ɗakin hutu ina shan shayi, na san dai an tafi da yaron waje, amma na yi zaton Baba aka Kai wa ya gan shi, ashe Ustaz ya zo tun kafin na sauka, sai ga shi ya shigo riƙe da yaron ya a murmushi, na haɗe rai, ya kalle ni ya ce"Sannu Assayyada, ya jikin naki?" Zuciyar musulunci ce kawai ta sa na daure na ce"Da sauƙi". Ya ce"Ma sha Allah, Allah Ya ƙara lafiya, na gode sosai Assayada, ashe ke ce za ki kawo min ɗana na farko? Alhamdulillah, wannan yaro ɗan gata ne, domin kuwa nan da wasu watanni za a yi masa ƙani ko ƙanwa, bi ma'ana yanzu haka matata tana da ciki a jikinta, kin san na yi aure kuwa?" Na ce"Malam ka yi abin da ya kawo ka kawai ka ajiye shi ka tafi". Ya ce"La ba'asa, Assayyada ba za ki canza hali ba ko? Ai kuwa ba fata nake yi miki ba za ki sha wahalar zaman aure, yanzu kin kammala iddarki Kenan na taya ki baƙinciki, sannan idan kin ga za ki koma ɗakinki ƙofa a buɗe take, duk da dai sai kin sha daga da matata, bi ma'ana Rauda tana sona tana kishina". Na yi tsaki na kau da kai gefe, ya ajiye ɗan yana cewa"Allah Ya raya Dawoud, bi ma'ana na saka masa sunan mahaifina". A daren 'yan'uwan Ustaz sun zo asibitin sun ga ɗa, Mama ta kwana da ni, washegari da safe aka sallame ni daga asibiti, muka koma gida Mama ta wanke mu tass ta gasa min jiki, sai ga Ustaz ya zo tare da babar shi da yar kula cike da naman kai mai romo da robar gurasa, ban yarda Ustaz ya gan ni ba, saboda har ga Allah ba na son ganin shi, duk da ta silar shi na samu cikar burina wato na haihu ni ma na samu gudan jinina. Kwana uku da haihuwar, da daddare muna zaune da Mama ina cin tuwo ita kuma tana goye da Dawoud muka ji sallama a tsakar gida, gabana ya ba da rass, don ko bayan shekara ɗari muryar Sadam ba za ta ɓace min ba, muƙutt na haɗiye lomar tuwon da na saka a bakinaeba tare da na tauna ba, da alama ita Mama ba ta gane muryar ba, sai ta amsa sallamar tana tambayar wane ne? "Mama Sadam ne, ina wuni". Ya faɗa kai tsaye. Mama ta zaro ido ta ce"Saddam!?" Tana yi min kallon hukuma. Jikina ya hau mazari, na fara in-ina da rawar baki na ce"Ban... Mama, wallahi ban san zai zo ba, ba ma waya na rantse da Allah". Mama ta yi huci mai zafi ta tashi ta fita daga ɗakin, ko kallon Saddam da ya rusuna yana gaishe ta ba ta yi ba, ta wuce shi, shi kuma kamar wanda aka yi masa iso ya shigo ɗakin da nake [02/11, 8:00 pm] Sadiya Abdulrazak: 34 Ya zauna yana kallona, na yunƙura zan tashi ya ce"Ina za ki je?" Na koma na ce"Sadam mene ne hakan? Me ya kawo ka gidan nan?" Ya ce"Da ke a waje kuma har a tambayi me ya kawo ni? Barka na zo, da kuma nunawa duniya ina jira ki kammala iddarki ne dama, ina fatan na wani ɗan iska da ya riga ni ko?" Na ce"Da ba ka zo yanzu ba, za a zargi akwai wata alaƙa tsakanina da kai bayan mutuwar aurena, sannan a ina ka san na haihu ma? Kuma ba ka tare da ni, da kana sona da za ka fahimce ni ba za ka ɗauki fushi da ni ba, ka nesanta kanka da ni, ni kuma a yanzu ba na buƙatarka ka bari Please ba yanzu ba". Ya tsaya yana kallona, fuskar shi babu yabo babu fallasa, kallon ya kashe min jiki, irin wanda na yi kewa ne, sai na sunkuyar da kai hawaye ya fara sakko min, wannan shi ne ga ƙoshi ga kwanan yunwa, ina farinciki da zuwan shi amma ya zama dole na nuna ban yi ba saboda iyayena su yarda da ni. Ya ce"Ki dakata da wannan pretending ɗin haka, kin san ina sonki, kin san ina tare da ke, sannan kina farinciki da zuwana yanzu ma, ban taɓa ganin ƙiyayyata a Idonki ba tun da na fara ganinki, ko a baya daƙiƙiyar ƙwaƙwalwarki ce ta ƙi ni ba ke da zuciyarki ba". Na ce"Na ji, ka tashi ka tafi, kar ka sake yi min irin wannan zuwan". Ya ce"Dama barka na zo, na kuma ga yanayin jikin naki, kin sauka lafiya?" Na ce"Lafiya lau". Ya ce"Allah Ya raya shi bisa sunna, hmm da ciwo a ce kin sakarwa wani jiki har kin haihu da shi, kin haifa masa ɗa ba nawa ba, kuma kina sane idan mace ta haihu jikinta canzawa yake yi, wannan yana ɗaya daga cikin dalilan da ya sa na ƙi ki haihu a farko, kike ganin hakan kamar ƙiyayya ko mugunta, ga shi kuma yanzu zan biya sabon sadaki na aure ki a duk yadda jikin naki ya zama". Na ce"Kana da raunin tunani ta wannan fannin kuwa, a tunaninka idan mace ba ta haihu ba shikenan jikinta ba zai taɓa canzawa ba?" A bazata na ji Mama ta ƙwala min kira"Sayyada!" Gabana ya faɗi, sai yanzu na gane ma na yi wauta da na zauna ina sauraron shi, ya miƙo min ledar da ya ajiye a kusa da shi ya ce"Ga wannan ba yawa, zan yi miki transfer wani abu, sannan duk abin da kike buƙata ki tambaye ni, sai mun yi waya". Ya fice daga ɗakin bai jira amsata ba, ina jiyo shi yana cewa Mama"Sai da safe, Allah Ya raya". Na yi zaton ma za ta dakatar da shi ta yi masa gargaɗi sai na ga saɓanin haka, ta shigo ɗakin ta rufe ni da faɗa kamar za ta dake ni, ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba, ta rantse sai na fito mata da wayar hannuna, na fara kuka na ce"Wallahi Mama ba ni da wata wayar bayan wacce kika karɓa, na rantse da Allah ba ni da wani connection da shi, ban san wanda ya faɗa masa na haihu ba, ban gayyace shi ba". Mama ta yi hau bincike kayana, tana watso su ƙasa, ni kuma sai kukan baƙinciki nake yi, a ce mahaifiyata tana zargina? Na shafawa kaina baƙin fenti, ta gama bincikenta tsaf ba ta samu komai ba, ta juyo tana yi min mugun kallo ta ce"Sayyada!" Na tsananta kuka na ce"Don Allah Mama ki yarda da ni". Ta ce"Ta ya zan yarda da ke? Me yasa zan yarda ba kwa waya alhalin jiya kika haihu yau ya ji labari har ya zo barka?" Na ce"Wallahi ba a wajena ya ji ba". Ta ce"Ina fatan dai ba ki manta alƙawarina a kan alaƙarki da shi ba ko? Babu ke babu auren shi har abada". Na kasa cewa komai, sai bugun zuciyata da ya canza, ta ce"Ki faɗa masa kar ya sake dawowa cikin gidan nan, idan kuma ya dawo laifinki ne, da ni kike zancen!". Na ce"Amma Mama ban san ta inda zan faɗa masa ba wallahi". Ta ce"Za ki sani ne idan ya sake dawowa". Ta fita daga ɗakin ta bar ni cikin zulumi, na rasa ya ma zan yi, haka na dinga fargabar kar ta faɗawa Baba, kuma na yi sa'a ba ta faɗa masa ɗin ba, can wajen goma na dare na janyo ledar da ya bar ta, Mama ta ganta amma ba ta bi ta kanta ba, na buɗe, da waya a kwali na fara cin karo gabana ya faɗi, na yi saurin rufe ledar, sai da na je banɗaki na yi fitsari na gyara jikina sannan na dawo na yi shirin bacci na rufe ɗakin na saka sakata, na buɗe ledar, na ciro wayar, na buɗe ta, na kunna, sai na ga da sim card a ciki, massage ya faɗo, na buɗe na ga an yi saving lambar da Mijina, "Idan kin kunna wayar ki kira ni". Abin da yake cikin saƙon kenan, na sauke numfashi, na ajiye ta a gefe na fara ciro kayan ciki, leses ne masu kyau da tsada guda uku sai takalmi da jaka, da wani box ɗin sarƙa mai shegen kyau, sai kuma kayan jariri kala uku masu kyau, jikina duk ya yi sanyi, har zuciyata ba na son kowa sai Sadam, da shi nake hasasho rayuwata ta gaba, ga kuma ƙudurin iyayena, ina tsoron fushinsu, tun da na san namiji ba shi da tabbas, na ga illar barin iyaye na zaɓi namiji, ba na fatan na maimaita, na kashe wayar na ɓoye ta, na gyara kayan da Mama ta watso min na kwanta, abunka da jikin jego sai bacci ya kwashe ni Ni mai nauyi, sai da yaron ya motsa sannan na farka na tashi zaune na shayar da shi, na fara tunanin Saddam yana can yana jiran kirana, amma ban yi nisa da tunanin ba bacci ya kwashe ni. Da safe Mama tana can tana kokawar dafa mana ruwan wanka na kunna wayar na kira shi, tun da ya zama dole na yi hakan saboda gudun kar ya dawo, ba ta daɗe tana ringing ba ya ɗauka da sallama, na amsa na gaishe shi, ya ce"Shi ne jiya kika bar ni da tunaninki ko? Me yasa ba ki kira ni ba?" Na ce"Sadam don girman kar ka sake zuwa gidanmu". Ya ce"Me yasa?" Na ce"Matsala za ka ja min a wajen iyayena, zargi suke ma ni ne na ce ka zo, don Allah kar ka sake zuwa". Ya ce"To yanzu dai dama ba zan zo ba sai bayan suna idan an yi arba'in haka, amma daina zuwa gabaɗaya kin san ba zai yiwu ba". Na ce"Zai yiwu". Ya ce"Ok kina nufin gidan shi harijin za ki koma kenan?" Na ce"Ba wanda zan aura, ai auren ba dole ba ne". Ya ce"Dole ne a gare ki, musamman da kika auri hariji kika sakar masa jiki har da haihuwa, yanzu sai jarumi ne ma zai iya zama da ke, ni ɗin ma zan gwada ne kawai". Na ce"Sai anjima, kar ka sake zuwa don Allah". Ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ya ce"Kina sona?" Na ce"Ba wannan maganar ce a gabana baz ka san dai ko zan yi aure sai na yaye ɗana ko? Ban tsara yin zance da wani ina shayarwa ba, don haka kar ka sake zuwa, kuma batun soyayya a ajiye shi a gefe, kafin ka hasala iyayena, su raba mu har abada tun kafin lokacin da ya kamata a fara batun auren ya yi". Ya sauke numfashi ya ce"Idan na fahimce ki dai kina sona, amma iyayenki ba sa sona kuma kina gudun fushinsu ko?" Na ce"Ina sonka Sadam, amma a wannan karon ba zan saɓa umarnin iyayena ba, duk yadda suka tsara min haka zan yi". Ya ce"Ko da ba su amince da aurenmu ba? Za ki zaɓi sake rayuwa da wanina a karo na biyu?" Na ce"Ba ni ce zan zaɓa ba, ƙaddara ce za ta zaɓar min". Ya ce"Shikanan, gara da kika faɗa min tun yanzu na janye jikina, na gode Sayyada ina yi miki fatan alkhairi". Na ce"Ba fa haka nake nufi ba". Ya ce"To faɗa min nufinki". Na ce"Kawai dai na san dole za a samu matsala ta wajen iyayena shiyasa nake faɗa maka haka". Ya ce"Tun da ba za ki iya fuskantar matsalar ba ki magance ta ai kin ga babu amfanin mu fara rayuwar da ba ta da ma'ana, tun da za mu ɓatawa juna lokaci ne kawai". Na ce"Ka dai tsaya mu ga abin da hali zai yi, amma kar ka dinga zuwa don Allah". Ya ce"Za mu dinga waya da chatting?" Na ce"E". Ya ce"Duk ranar da ban ji ki ba zan zo kin yarda?" Na ce"Na yarda, amma kar ka dinga kira saboda tsaro, idan na samu space zan dinga taɓo ka". Ya ce"Ok, I love you, you are mine". Na ce"Love you too". Na kashe wayar na ajiye, na lumshe ido ina tuna lokacin da nake gidan shi kafin al'amura su fara lalacewa. A haka Mama ta shigo ta same ni, ta ɗauki ɗan tana ce min"Ki je na kai miki ruwan ki shiga". Na gama komai na shirya ina karyawa sai ga sallamar Ustaz, ina jin Mama tana ba shi izinin shigowa na fizgo mayafi na lulluɓe jikina, na ɓata rai sosai, na ji alamar dai ya shiga ɗakin Mama, ba jimawa kuma ya yi sallama a ɗakin da nake, na sake haɗe fuska, sannan na amsa, ya ce"Zan iya shigowa?" Na ƙi amsawa. Ya ɗan yi sakanni sannan ya shigo yana ƙara sallama, hannunsa riƙe da jaririn ya ce"Haba ya ke Assayyada ya ina neman kuma kin ƙu amsawa? Kin san yanzu ke ba matata ba ce, iddar ma da nake tunawa kina ciki na ji daɗi yanzu an ƙare ta, don haka dole na nemi izininki yayinda zan shigo inda kike, don gudun saɓawa shari'a, bi ma'ana kar na yi tozali da abin da bai halatta na gani ba". 'Hali yana nan' Na faɗa a zuciyata. A fili kuwa na kau da kai na ce"Ina kwana". Ya ce"Lafiya lau Assayyada, Alhamdulillah, ya ƙarfin jiki, ya kwanan Abiy? Bi ma'ana takwaran mahaifina". Na ce"Ƙalau". Ya ce"Ma sha Allah, dama na zo ne na gan shi ke ma na ga jikin naki". Na ce"Ka tsaya a iya ɗan naka, don ni dai ba Ni da wata alaƙa da kai". Ya ce"Hakane, amma ni na yi zaton zuwa yanzu kin huce za mu sasanta amma fa ba wai na damu ba ne, dama makomar wannan yaron nake dubawa". Na ce"Kar ka saka ran za mu sasanta har abada, da ma can ban so ka ba, kuma ba zan taɓa sonka ba har abada". Ya ce"Subhanallah, abun bai kai haka ba Assayyada, kuma yanzu rayuwa ta canza, na wuce wannan wulaƙancin in sha Allah, gaba kaɗan zan auri kamar ki biyu a rana ɗaya, ke kuma Allah Ya ba ki kalar wanda kike so". Na amsa da Amin, ya yi min sallama ya tafi, tun daga ranar kuma idan ya zo ba ya ganina ɗan kawai yake gani ya tafi, ana jibi suna 'yan'uwan shi suka kawo kayan barka, sun yi ƙoƙari ba laifi, ni ma sun haɗo min da atamfa guda biyu, sannan dangina ma sun yi mana kaya ni da Dawoud, amma duk da haka sai da na ciri kuɗi na bawa ƙanwata Khadija na lissafa wasu abubuwan da nake so, ranar suna Ustaz ya kawo rago babba, don mahaifin Rauda ne ya ba shi kyautarsa, duk yadda ya yi da Rauda ta je barka ta ƙi, saboda da gaske take kishinsa, tana ta rainon cikinta ita ma, zuwa yanzu har ta fara sabawa da halin Ustaz na mammaƙo, ta riga ta gane ƙarya kawai yake yi ba wata ulcer da ta hana shi cin wasu abubuwa, don haka idan tana son cin abu sai ta siya da kuɗinta ta daga ta ci, saboda kar ta mora ta koyi taune ƙashi ta tsotse, tun da ta gane idan ta ci nama dare yake bi ya taune ƙashin. Ita dai tana son shi, don haka ta ga za ta iya daurewa ta zauna da shi, musamman yanzu da ta zama irin jinsin shi, ƙarfi da yaji ya mai da ita wata ƙaramar harija, dole ne yanzu kullum sai ta neme shi, wataran ma sai biyu a rana, shi yasa Ustaz bajau da shi. Tun da aka yi taron suna 'yan barka suka ɗauke ƙafa sai na samu kaɗaici, don ma dai kullum sai mun yi waya da Sadam da daddare, da rana ma idan na ga Mama ta yi bacci muna yi, ko mu yi chatting, hankali kwance muke farfaɗo da soyayyarmu tare da gina ta da wasu kayan aiki masu ƙarfin da rushe wannan soyayya zai yi wahala, muna ta samun shaƙuwa da shi. Sanda na yi arba'in zan je kai Abiy allura, Sadam ya ce ya kamata mu haɗu, ban yi musu ba saboda ni kaina ina kewar shi, ina son ganin shi a zahiri mu gana, ranar na yi kwalliyar da rabona da yi tun ranar suna, na goya ɗaya, na yafa mayafi na tafi asibiti, ina cikin asibitin ya kira ni ya ce ya ƙaraso yana ƙofar asibitin, da na gama na same shi a tsaye a jikin motarsa, sai ya shiga, ni ma na buɗe na shiga, ya ja motar muka fara tafiya, na kalle shi na ce"Ina za mu je?" Ya yi murmushi ya ce"Siyar da ke zan yi". Na yi 'yar dariya na ce"Ai ni ba zan saidu ba". Ya ce"To mu je gidana ki rage min zafi, ganin ki ya birkita ni". Fara'ar fuskata ta ɗauke, raina kuma ya ɓaci. Ya ce"Saki fuskar Babyna, wasa nake yi miki, amma da gaske fa a yanzu ke kaɗai nake gani ki birkita min lissafi na ji ni namiji ne". Na ce "To na ji a bar zancen". Ya ce"An bar shi". Ya karkata motar muka shiga wata unguwa, ya samu wajen wata bishiya ya yi packing, ya kashe motar ya kalle ni yana murmushi ya ce"Sayyadata, ya garin?" Na ce"Lafiya lau". Ya ce"Na ji daɗin ganinki sosai fa". Na ce"Ni ma haka". Ya ce"Sai yaushe za ki yaye yaron naki?" Na ce "Ai da saura, a ƙalla dai ya yi wata sha shida". Ya yi tsaki ya ce"Gaskiya ya yi tsayi, gabaɗaya wannan ɗan iskan harijin ya canza min lissafi, kuma ke ce kika bawa abun goyon baya". Na ce"Haka Allah Ya tsara, ka daina cewa haka". Ya ɗaga kai yana kallon saman motar, yaron ya fara 'yan ƙananun kuka, na sauke shi, Sadam ya kalle shi ya taɓe baki ya ce"Ɗan ƙaddara kenan". Maganar ta zo min a bazata, kuma ta yi min zafi, sam ban ji daɗi ba, amma na maze ban ce komai ba, na saka shi a kafaɗa ina rarrashin sa amma ya ƙi yin shiru, da alama dai yunwa yake ji, a dole na sauke shi na ɗora a cinyata na fara shayar da shi bayan na lulluɓe shi da mayafina, kunya duk ta kama ni. Ban san kallona yake yi ba sai da na ji ya ce"Abin da kike rufewar wane ne baƙon shi? Indai ba canza ki aka yi ba ai kin san ni na fara sanin shi ko? Idan ma za ki jiki ko buɗe ki saki Malama". Wannan yana daga cikin dalilin da ya sa na tsara ba zan yi soyayya ina shayarwa ba, tun da dole yaro zai buƙaci abincinsa, shayarwa a gaban wanda ba mahaifinsa ba kuwa yana iya haddasa abubuwa da dama, na yi shiru kamar ban ji shi ba, shi ma bai sake cewa komai ba, har yaron ya ƙoshi, na saka shi a kafaɗa, ya sauke numfashi ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ya ce"Don Allah ko da lokaci ya yi idan aka hana ki aurena kar ki yarda, saboda idan ba ko aure ni ba zan cutu". Na ce "Ni ma zan cutu sosai, in sha Allah ma ba za su hana ba, amma ka yi haƙuri idan sun hana mu haƙura kawai, saboda na yi alƙawarin ba zan sake saɓawa iyayena ba". Ya ce"Ok". Muka taɓa fira, ina ta jijjiga ɗana, amma Saddam ko ya ce ya sunan shi ballantana ma ya ɗauke shi, ban ji daɗin haka ba, har muka rabu bai ɗauki ɗan nan ba. Na tari adaidaitasahu na koma gida, zuciyata fara ƙal saboda na ji daɗin ganin shi, sai na ji na ƙagauta wata allurar ta zagayo saboda mu sake irin wannan haɗuwar. 08028966015 [03/11, 7:29 pm] Sadiya Abdulrazak: 35 Idan Ustaz ya bushi iskar shi yana zuwa ya ga ɗan shi, har ma ya ba da kuɗi ya ce a siya masa pampars, ina nan ina ɓoyayyiyar soyayyata da Sadam, watarana ina zaune Mama ta ɗakko wayata ta ba ni, ta ce"Ga wayarki nan Sayyada, zan saka babanku ya siya miki sabon layi, ruwanki ne ki cigaba da shashancin da ba zai amfani rayuwarki ba, ruwanki ne kuma ki nutsu ki san inda yake yi miki ciwo, ki kawo miji ko wane ne, amma ban da Sadam, ba za ki aure shi ba indai ina raye". Zuciyata ta tsinke, idona ya kawo ruwa amma ban bari ya sakko ba, babban kalmar da take rusa nutsuwata ita ce ba zan auri Sadam ba, haka na karɓi wayar na ajiye, washegari Baba ya kawo min sabon layi, sai na fara amfani da wayar ina rabawa mutane lambar, tun da ita ta wajen Sadam da shi kaɗai nake magana. Da lokacin komawa kai Abiy allura ya yi, muka sake shirya haɗuwa, muka yi kamar yadda muka yi a wancen lokacin, muka sha firarmu a mota, a wannan karon ma nunawa ya yi kamar bai ga ɗana ba, na kasa haƙuri sai da na ce"Ba ka ga Abiy ba wai? Ba ka taɓa ɗaukar shi ba". Ya yi gajeren tsaki ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ya ce"Bari na faɗa miki gaskiya, da ina da ikon goge sunanki daga mahaifiyar yaron nan da na yi, ba ni da alaƙa da ɗanki ta kusa ko ta nesa, don haka ke nake so ba shi ba". Na yi mamakin maganarsa, kuma ban ji daɗinta ba, na ce"Amma ai an ce maso uwa ya so 'ya'yanta, Sadam ya kyautu ka ce ba ka da alaƙa ko ta nesa da shi? Daga jikin wacce kake so fa ya fito, jinina ne". Ya taɓa baki ya ce"Amma dai kin san ba a so dole ko? To idan dole za ki yi min na so shi sai ki buɗe zuciyata ki saka min, ba na son duk wani abu da zai saka na tuna kin yi rayuwar aure da wani ba ni ba". Na ce"Amma yanzu kenan ko aurenmu muka yi ba za ka riƙe min ɗana ba?" Ya ce"Gaskiya dai, ko da ubansa ba ya raye sai dai a bawa dangi shi, ba zan riƙe agola ba". Da mamaki na ce"Amma idan ka rabu da matarka fa? Kenan ba za iya ba ni riƙon 'yarka ba?" Ya ce"Ya zama dole ki riƙe, kamar yadda ya zama dole matar uban ɗanki ta riƙe miki ɗa, ni kalmar agola ce ba na so, kowane ɗa ya fi kyau da gidan ubansa, ko ba ki an ce da uba ake ado ba? Kuma kyaun ɗa ya gaji ubansa". Jikina duk sai ya yi sanyi, hankalina ya fara tashi, don ni a shirina da ɗana zan tafi duk inda zan je, na sauke numfashi na ce"Wannan tsarin naka ba shi da wata alaƙa da kalmar da uba ake ado, shikenan Allah Ya zaɓa abin da ya fi alkhairi". Na buɗe murfin motar zan fita, ya riƙo hannuna, na dakata na juyo na kalle shi, ya ce"Wai fushi kika yi?" Na ce"A'a". Ya ce"Fushi kika yi mana, amma na yi mamaki kuwa, da kika ce Allah Ya zaɓa abin da yake alkhairi me kike nufi? Kenan za ki iya fasa aurena don na ce ba zan riƙe ɗanki ba?" Na ce"Ba zan fasa aurenka bisa wannan dalilin ba, tun da ai kana kan gaskiyarka ba hakkinka ba ne ka riƙe shi, sai dai sam ba ka yi min kara ba Saddam". Ya ce"Ki yi haƙuri, na kasa sarrafa kishina ne, ina son ki Sayyada, kallon yaron zai dinga tunzura kishina, wallahi ƙiyayyar da na yi wa baban shi za ta shafe shi na zo ina cutar da shi, kin ga maganin kar a yi kar a fara ko?" Na jinjina kai na ce"Hakane, zan tafi". Ya ce"Ba za ki tafi ba, sai kin huce, na ga kin ɗauki fushi da ni". Na ce"Zan huce daga baya, ai na daina dogon fushi da kai". Na yi ƙoƙarin zame hannuna da ya riƙe, ya ƙi saki, na juyo na kalle shi, idanunsa suka karantar da ni yanayin da ya shiga, tun da ba yau na san shi ba, na ce"Sake ni Sadam kar Mama ta ga na daɗe". Ya ce"Hannunki ya rage laushi, me yasa?" Na fizge na ce"Kai ka ji haka". Na fita daga motar na tafi, ko sallama bai yi min ba, saboda yanayin da yake ciki, na koma gida jikina a mace, ko da ya riƙe hannuna ban ji wani abu ba, sannan shigar shi wannan yanayin bai sa ni ma na ji sha'awar kasancewa da shi ba, ni tun bayan rabuwa da Ustaz ma ban ƙara jin sha'awar sex ba, shi yasa nake tunanin kawai ya kashe min sha'awa ne. Ina son Sadam, ina fargabar wataran shaiɗan ya saka shi abin da ba zan so ba, alƙawari ba yi na bar saɓawa Allah ta hanyar zina, ba na fatan na sake aikatawa, don haka na fara shakkar haɗuwarmu da shi. Duk yadda zuciya take faɗa min Sadam ba masoyi ba ne tun da ba ya son ɗana, haka na dinga ba ta uzurin kishi ne ya ja haka, kuma sai da so ake kishi, sannan ba dole ba ne don kana son uwa ka so ɗanta. Mun cigaba da soyayya ta waya, amma na daure zuciyata ban sake bari mun haɗu da shi ba, idan zan kai Abiy allura ba na faɗa masa, da ya tuhume ni na ce masa na daina kai shi saboda tana saka shi kuka, sai ya fara neman mu haɗu a wani wajen, nan ma na dinga fizgewa na nuna masa kwata-kwata ba na fita ko'ina, duk nacinsa na ƙi yarda mu haɗu, a shirina sai na yaye ɗana, na shirya auren, sai ya fara zuwa idan Allah Ya da iyaye sun amince da wuri sai a saka rana kadan a yi auren kowa ya huta. Mun yi wata uku ba mu haɗu da shi ba, wanda ya yi daidai da watannin ɗana shida, ni kaina ina son ganin shi, amma ba na son kusancinmu, wataran da daddare bayan sallar isha'i duka muna tsakar gida har da Baba kawai sai ga yaro wai ana sallama da Sayyada, gabana ya ba da rass, duk da ban ma kawo Saddam ba ne, Mama ta kalle ni, Baba kuwa ya cigaba da cin abincinsa, ganin na yi shiru kuma ba ni da niyyar motsawa Baba ya ce"Sayyada ba da ke ake sallama ba?". Na ce"Baba ai ban san ko wane ne ba". Mama ta ce da dan aiken"Je ka tambayo wane ne". Gabana ya shiga dukan tara-tara, ga Mama sai kallon tuhuma take yi min, na sunkuyar da kai ina wasa da hannun Abiy da ke zaune a kusa da ni, yaron ya dawo ya ce"Ya ce wai Isma'il ne". Baba ya ce"Ka ce tana zuwa". Sannan ya ce"Wa kuma kika samo?" Na ce"Wallahi ban san shi ba, ba na kula kowa kuma ban haɗu da kowa ba". Ya ce"Ai ba laifi ba ne, ki je ki gani". Na shiga ɗaki na sako hijjabi na fita, Abiy yana miƙo min hannu ban ɗauke shi ba, Mama ta ɗauke shi, ina fita ƙofar gidan tun kafin na gan shi na ji ƙamshin turarensa, gabana ya tsananta faɗuwa, na ƙarasa inda yake zaune a babur na ce"Sadam, me ya kawo ka?" Ya ce"Babu sallama ballantana gaisuwa?" Na ce"Don Allah me yasa ka zo? Baba ma yana nan fa". Ya ce"Sayyada har yaushe za mu kai muna ɓoye soyayyar nan ne?" Na ce"Amma ai na faɗa maka sai na yaye ɗana zan yi aure". Ya ce"Yanzu ya dace mu fito da soyayyar, sai a fara gwagwarmayar kafin ki yaye, kin ga zuwa lokacin kowa ya gaji ya sakar mana, kina yayewa sai batun auren kawai". Na ce"A'a don Allah ka daina cewa haka, gaskiya ba yanzu ba, ban shirya ba tukuna". Bai kula maganata ba, sai ƙure ni da kallo da ya yi, ya ce"Duk kin rame, yaro ya zuƙe ki sai yaushe za ki yaye shi?" Kamar zan yi kuka na ce"Ka tafi Sadam don Allah". Ya ce"Ba zan tafi ba, kuma yanzu ma na fara zuwa". Na ce"Za ka ja min matsala". Ya ce"To a ina za mu haɗu?" Na ce"Nan da sati biyu zan je asibiti sai mu haɗu". Ya ce"Kin yi alƙawarin za ki sanar da ni mu haɗu?" Na ce"Wallahi na yi". Ya ce"Kuɗin hayar gidanki na ajiye miki ko na turo miki?" Na ce"Ban gane ba". Ya ce"Ok idan mun yi waya zan yi miki bayani, yanzu na tafi ba kya son ganina ko?" Na ce"Ba haka ba ne, amma tsoro nake ji shiyasa". Ya ce"Ok, sai anjima, i love You". Ya ce"Ba za ki mayar min ba?" Na ce"Ni dai ka tafi". Ya ce"Ai kuwa ba ki so na tafi ba, wallahi sai kin faɗs zan tafi". Yana rufe baki na ce"I love You". Ya buga babur ɗin ya tafi, na dafe ƙirji, ina lumshe ido, na yi 'yan sakanni a haka sannan na shiga gida. Ina shiga Mama ta ce"Wane ne shi? Kuma daga ina?" Na ce"Wani ne, ban san daga inda yake ba". Ta ce"To me ya kawo shi?" Na ce"Na faɗa masa ba aure zan yi yanzu ba, sai na yaye". Na shige ɗaki ban jira wata tambayar ba. Wajen goma na dare Sadam ya kira ni, muka gaisa na ce"Ka je gida lafiya" Ya ce"Lafiya lau, kin ga alert?" Na ce"A'a, layin da nake ganin alert ɗin yanzu babu". Ya ce"Ok na saka miki kuɗinki, dubu ɗari shida". Na ce"Ni fa ban gane ba, wai da gaske ka bar min gidanka?" Ya ce"In sha Allah! Ko yanzu kike so zan kawo miki takardun gidan, idan kin shirya a canza sunan zuwa naki". Na ce"A'a, amma Sadam a kan me za ka ba ni gida?" Ya ce"Saboda kin cancanta ne". Na ce"Kyautar ta yi nauyi, na zai yiwu ba". Ya ce"A bar zancen, yanzu ni a wane matsayi kika ajiye ni? A wace Larabar nake Sayyadata?" Na ce"A cikin zuciyata kake". Ya ce"Kuma na zo kika kore ni? Duk na rikice". Na ce"Tsoro nake, amma in sha Allah da na yaye yaron nan komai zai daidaita". Ya ce"Zan fara ƙirgen kwanaki har zuwa sati biyun". Na ce"In sha Allah za mu haɗu, ai kamar yau ne". Na ce"Ina matarka ne, ko ba ka gida?" Ya ce"Ina gida mana, ga ta kusa da ni ma yanzu ta biyo ni ɗakin". Kishi ya kama ni na ce"To sai anjima". Ya ce"A kan me? Ba fa yau muka fara waya da ke a gabanta ba". Na ce"Kuma ba ta damuw?" Ya ce"To idan ma ta damu ya za ta yi? Ko za ta hana ni ne?" Na ce"A'a". Muka taɓa fira muka yi sallama, ina jin bai kyautawa matarsa ba, ta wani fannin kuma daɗi nake ji, tun da ita ma kafin aurensu haka take yi min ai. Tsakanin ni da shi ban san wanda ya fi wani zumuɗin cikar sati biyun ba, da ranar ta zo na yi kwalliya na tafi asibiti, bayan na gama kamar yadda na saba na fito na tarar da shi, na buɗe motarsa na shiga muka fara tafiya, a daidai inda muka saba tsayawa ya faka motar, ya kalle ni ya ce"Sayyadata". Na ce"Na'am". Ya ce"Kina azabtar da ni sosai fa, na gaji da wannan jiran, da kin cire cikin da tuni yanzu kina gidana". Na ce"Haka Allah Ya tsara". Daidai nan adaidaitasahu ta ƙaraso wajen motar, Safna ta fito da sauri kamar za ta kifa, ta shiga ƙwanƙwasawa babu ƙaƙƙautawa, gaban Sayyada ya faɗi, Sadam yana kallon glass ɗin ya ga Safna shi ma gabansa ya faɗi, ɓacin rai ya lulluɓe shi, Safna ta buɗe murfin motar ta fizgo Sayyada, har Abiy ya gwara kanshi, amma dai ba ta fito da ita ba, Sadam ya fita daga motar, ya wanke Safna da mari ya ce"Ba ki da hankali? Ni sa'anki ne da za ki dinga bibiyata?" Ta fara kuka ta ce"An bibiye ka ɗin, munafukan banza da wofi, ashe a nan kuke haɗuwa? Uban me kuke yi a mota?" Ya ce"Ubanki muke yi da kaza-kazanki, ki shige ki tafi gida ko ranki ya yi mummunan ɓaci". Ta ce"Ba zan tafi ba! Ka daɗe ba ka ɓata min rai ba, munafiki kawai, dama tun da aurenta kake bibiyarta, to wallahi indai ka ce za ka dawo da ita sai an yi bala'in da ba ka taɓa gani ba". Ya ce"To ki fara yi tun yanzu, don Sayyada kamar na aure ta, kuma a kanta zan iya rabuwa da ke, don ta fi ki amfani a wajena". Ina motar ina kuka, ganin mutane sun fara taruwa na ji tsoro kar wanda ya san ni ya zo wajen a kai labari gida na shiga uku, ga shi ko niƙabi ban saka ba, don haka na fito daga motar ɗauke da ɗana, Saddam ya ce"Ki koma ki zauna". Na ce"Ka rabu da ni gida zan tafi". Ya ce"Ni ma gidan zan mayar da ke". Na girgiza masa kai alamar a'a, na fara tafiya, duk yadda ya so ya tsayar da ni na ƙi tsayawa, na hau adaidaitasahun ya ja muka tafi, ya shiga motarsa shi ma rai a ɓace, ya bar Safna tsaye a wajen tana cigaba da zagina, kafin ita ma ta shiga adaidaitasahun ta bi bayana. Ban san tana biye da ni ba sai na sauka a ƙofar gida, na ita ma ta fito daga adaidaitasahun, gabana ya yi mummunar faɗuwa, na ce"Me kika biyo ni ki yi min? Indai mijinki ne na rabu da shi, na bar miki". Ta ce"Uwarki da ubanki na zo yi wa gargaɗi ai ba ke ba, don su ne sa'annin yina". Hankalina ya tashi kamar zan yi kuka na ce"Don Allah ki yi haƙuri, wallahi na rabu da shi indai Saddam ne". Ta bangaje ni ta shiga cikin gidan, na mara mata ina kukan nadamar fita a yau ɗin ma bakiɗaya, Mama ta miƙe tsaye a razane ganinmu wujiga-wujiga ta ce"Sayyada lafiya?" Safna ta ce"Zuwa na yi na yi muku gargaɗi na farko kuma na karshe a kan mijina, ki raba kwartuwar 'yarki da bibiyar mijina, idan ba haka ba komai zai iya faruwa". Mama ta ce"Ban gane ba me kike nufi?" Safna ta ce"Tun kafin ƙaddararren aurenta ya mutu take bibiyar mijina, ina ta haƙuri, yanzu ma kullum sai sun yi waya da shi a gabana, sannan yau na same su a cikin mota suna aikata son ransu, kuma ba wannan ne karo na farko da suke haɗuwa ba, ko a hotels ko a gidana, yau abun ma ya kai ba za su iya haƙuri su ƙarasa wani wajen ba shi ne suka keɓe a mota...!". Tana zuwa daidai nan na shiga ɗakina da gudu, na ajiye Abiy na rushe da kuka, sannan na lalubi wayata a jaka na kira shi, yana ɗagawa na rushe da kuka na ce"Ka cuce ni da ka sa muka haɗu yau, ga matarka nan ta biyo ni har gida tana yi mana ƙazafin wai muna aikata ma sha'a, na shiga uku Saddam, silarka iyayena za su ƙara ganin baƙina". Ransa ya yi mugun ɓaci, ya ce"Safnan ce ta zo gidanku? Yanzu ta tafi ko tana nan?" Na ce"Ba ta tafi ba, ta riga ta gama lalata ni a idon uwata, ya zan yi da rayuwata wane bayanin zan yi a fahimce ni?" Ya ce"Sayyada, ki fita ki faɗawa Safna ni mijinta Sadam na sake ta!". Na kashe wayar na zauna ina ta kuka, har ta gama bambaminta, Mama tana ta ba ta haƙuri ta bar gidan. 08028966015 [04/11, 7:42 pm] Sadiya Abdulrazak: 36 Tana tafiya Mama ta faɗo ɗakin da nake, gabana ya yi mummunan faɗuwa ganinta da taɓarya ta tunkaro ni, na miƙe tsaye ina"Ki yi Mama don Allah, kar ki kashe ni na rayata a wuyanki, wannan shi ne ƙaddarata". Allah Ya taimake ni ta jefar da taɓaryar ta yi kaina, na maƙale a kusurwar ɗaki, ba zan tuna yaushe rabon da Mama ta dake ni ba, tun ina yarinya sosai, amma yau haka ta rufe ni da duka ta ko'ina, ina ta gursheƙen kuka, amma ba na zafin dukan ba, na jin haushin kaina a kan ɓata mata rai, da kuma tausayin kaina, saboda idan na rabu da Saddam ba na jin zan sake yin aure, sai yanzu na gane abin da yasa ake cewa mace ta yi haƙuri da mijinta, inda na san zan so Sadam bayan rabuwarmu kuma ba zan samu kamar shi ba, da na haƙura a wancen lokacin mun cigaba da zaman ko babu daɗi. Da ta gaji da dukana sai ta fashe da kuka ta bar ɗakin, na rarrafa na ɗauki Abiy da yake ta kukan shi ma, na rungume shi na cigaba da kukana, har ya yi bacci, ina ji kira yana ta shigowa wayata, kuma na san Sadam ne, amma ban ma duba ba ballantana na ɗauka, nadama duk ta rufe ni, ban sake jin motsin Mama ba, sai da aka kira sallar azhar, na ji ta fito tana zuba ruwa a buta da alama alwala take yi, na kwantar da Abiy ni ma na fito bayan ta koma ɗaki, na yi alwalar na yi sallah kaina sai ciwo yake yi, wajen ƙarfe biyu da rabi na gane Mama ba za ta yi girki ba, na fita na shiga ɗakin nata, na tsugunna rakuɓe a jikin labule kaina a ƙasa na ce"Mama don Allah ki yi haƙuri ki yafe min, in sha Allah ba zan sake wannan kuskuren ma, kuma wallahi matar nan sharri ta yi min, na rantse da Allah ƙarya take, na san dai mun haɗu amma wallahi a kan hanya ne, ba mu taɓa zuwa wani waje ba". Ƙala ba ta ce min ba, har na ƙaraci tsugunon na tashi, na ce"Me zan dafa miki?" Nan ma ba ta kalle ni ba, na fito na kunna wuta na ɗora, jollof ɗin taliya na yi, har na gama ba ta ce min komai ba, na zuba na kai mata, na bar ɗakin, don ita na yi, ni ko yunwar ma ba na ji, na yi wanka na sha magani na kwanta, da na tuna ƙila fa aurena da Saddam ba zai yiwu ba sai hawaye ya ɓalle min, na wuni a ɗaki, zuwa la'asar na fita daga gidan, na siya awara da lemo, na ci na zauna jugum ina jiran dawowar Baba, duk da ina kokonton za ta faɗa masa ko za ta rufa min asiri? Baba yana dawowa bugun zuciyata ya canza, na yi tsuru-tsuru, na kasa fita na yi masa sannu da zuwa, ina jin lokacin da yake tambayar Mama me yake damunta? Gabana ya ba da rass, na miƙe tsaye, ban ji dai muryarta ba, amma na ji shiru, kafin kuma na ji Baba ya ƙwalla min kira cikin ɗaga murya"Sayyada! Ke Sayyada!". Na ɗora hannu a ka, ina jin kamar na yi tsuntsuwa na bar gidan, sai da ya sake kirana sannan na fito, na rakuɓe nesa da su na ce"Baba sannu da zuwa". Bai amsa ba ya ce"Zo nan Sayyada". Na ƙarasa gaban shi na durƙusa ina kallon ƙasa, ban ankara ba na ji saukar mari a fuskata tass, na gigice na fara kuka, na ce"Don Allah ku yi haƙuri, in sha Allah ba zan sake ba, kuma wallahi sharri ta yi min ƙarya take". Ya ce"Yi min shiru! Mutuniyar banza, wato dai idan aka cire maka Zakka a gida babu yadda za ka yi sai ka ba da zakkar nan, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Sayyada so kike wani ciwon ya kama mahaifiyarki? Don wallahi ita abun ya fi damu, ni dai don na yafe ki har lahira ba komai ba ne a wajena, ashe tun kina cikin idda kike tare da shi?" Ya kalli Mama ya ce"Wallahi ke ma da laifinki tun da dai har ya zo gidan nan da sunan zuwa barka ba ki faɗa min ba, tukunna ma, ba kya ɗaukar taɓarya ki sheme ƙafar ɗan banza? Kai Allah wadaran naka ya lalace". Ni dai sai kuka nake yi kaina a ƙasa. Ya ce"Gobe da kaina zan kai ki asibiti a yi miki gwajin ciki, idan aka samu babu to barkanki, kuma ki sani ba za ki sake fita ko ƙofar gida ba sai ranar aurenki, ko manemi kika samu na yi alƙawarin sai dai ku dinga zance a cikin gidan nan". Na ce"Don Allah ku yi haƙuri". Ya ce"Haƙuri ke ya kama, kuma kanki kika cuta Sayyada, ke kanki ba ki san ki yi wa adalci ba, ballantana mu iyayenki, idan kin yi mana kin rabu da shi ruwanki, idan kuma kin ga ba za ki iya rabuwa da shi ba to ki shiga duniya kawai, domin ba zan taɓa sauka a kan bakana ba, ke da Sadam kun gama zaman aure". Wani abu ne yake cakar zuciyata idan na ji an ambaci rabuwata da Saddam, amma haka na daure ban musa ba, ya yi faɗan shi ya gaji don kan shi, ya ce na tashi na ba shi waje, na shiga ɗakina na rushe da kuka, daidai nan kiran Sadam ya shigo. Na ɗaga ina tsananta kukana, ya yi shiru yana saurarona, ganin abun ba na ƙarau ba ne ya sa shi faɗin"Ya isa haka Sayyada, kukan kuma na mene ne?" Na ce"Ai ka fi ni sani". Ya ce"To ba ya wuce ba? Na sake ta, kuma idan kin ga na dawo da ita to kin tabbatar min ba za ki aure ni ba ne, ke sai dai ma na auri wata, amma Safna na gama zama da ita in sha Allah, tun da na yi mata hukunci mafi tsauri ai ya kamata ki huce ko?" Na ce"Ba kukan abin da ta yi min nake yi ba, kukan ɓatawa iyayena rai nake, an dake ni an yi min faɗa, na yi nadamar fitowa yau". Ya ce"To ya zamu yi? Ni ma dukana ne kawai ba a yi ba, tun da daga gidan naku gidanmu ta wuce, to amma ya za mu yi? Matuƙar ba guduwa za mu yi wani wajen mu yi auren sirri ba ya zama dole mu fito mu nunawa duniya da su iyayen namu muna tare, kuma ba za mu rabu ba duk runtsi, wallahi Sayyada idan ba mu yi aure ba ke kika so". Na ce"Ai ka san ba zan so haka ba sai idan ya zama dole". Ya ce"Idan na zo zance kika fita, gobe ma kika fita ko dukanki suke idan kika dawo haka za ki daure, dole za su gaji, idan kuma suka ɗaure ki sai ki ƙi kula kowa da auren, ai ba za su kwaɗa ki su cinye ba ko? Da a ce kin auri wani ai gara ni da ke ɗin mu rayu ba mu sake yin auren ba, ni dai idan kin ga na yi aure to kin saɓa alƙawarinmu ne kin yi, daga nan na san ba kya tare da ni". Na ce"Ina tare da kai har abada Sadam". Ya ce"To gobe zan zo zance". Na ce"A'a don Allah!". Ya ce"Zan zo". Ya kashe kiran, na kira ya ƙi ɗauka, na bi shi da saƙo ina roƙon shi kar ya zo, haka na kwana rai babu daɗi. Washegari har na manta da furucin Baba na cewar zai kai ni asibiti, sai ga shi ya ce na shirya mu je, na ce"Wallahi Baba sharri ta yi mana, ba wani abu da ya taɓa shiga tsakaninmu". Ya daka min tsawa rai a ɓace ya ce"Kin wuce mun tafi ko sai na targaɗa ki?" Na saka hijjabi na goya ɗana muka tafi, ina ta hawaye a adaidaitasahu, sai da aka yi gwajin sannan Baba ya yarda, muna dawowa gida ya na zauna a tsakar gida, na zauna ya ce da Mama"Maza shiga ɗakinta ki bincike min shi tsaf, ki kawo min wayarta da katin cirar kuɗinta, ko caza kar ki bari". Mama ta shiga ta bincika, sai ga ta ta fito da wayoyina biyu har da kwalin sabuwar, da kuma ATM ɗin, ta kalle ni ta ce"Yaushe kika siya sabuwar waya?" Na sunkuyar da kai. Baba ya ce"Har kya tsaya tambaya? Shi ya ba ta, shi ne ya ba ta, wa zai ba ta? Lallai ka ji tsoron Allah, ka ji tsoron yaran zamani". Ya ce"Sayyada idan kin yarda ni ubanki ne, to daga yau na raba ki da Sadam, kuma na haramta miki fita ko'ina, ko ƙofar gida ban yarda ki fita ba, kina yaye yaron nan zan samo miki mijin da ya dace da ke ki yi aure, idan kika taka dokata dama tun kafin na ji labari ki tabbatar kin haɗa kayanki kin bar gidan nan, don haɗuwata da ke ba za ta yi miki daɗi ba". Na tashi na shiga ɗakin, na hau gyara kayana ina kuka, haka na yi wunin ƙungi, Mama ta ɗauke min wuta, da daddare sai ga yaro wai ana sallama da Sayyada injiSadam, ga shi Baba yana nan, ya tashi ya fita, ban san dai ya suka yi ba, amma na tabbata ba magana me daɗi zai faɗa masa ba. Babu ta inda nake jin sassauci, na rasa ya zan yi, sati ɗayan da na yi na Sadam ba waya sai na ji kamar ba na raye, ni kaɗai na san uƙubar da nake ji a zuciyata, haka na fara gudanar da sabuwar rayuwa mai cike da kewar Sadam, cikin zuciyata kuwa na ƙudurce zan rayu babu aure, matuƙar Baba ba zai yi min auren dole ba, duk wanda ya kawo min zan ce bai yi min ba har ya haƙura ya daina kawowa. Da zaman kaɗaici ya ishe ni, wataran na roƙi Baba na ce don Allah ya siya min rediyo, ya siyo min 'yar madaidaiciya, na dinga saurara, daga wannan tashar na koma wancen. USTAZ A kwana a tashi lokacin haihuwar Rauda ya yi, haihuwar ta zo mata da sauƙi, don da asuba ma sun kashe arna, kuma da safe wajen ƙarfe sha ɗaya ta haifi ɗanta namiji, Ustaz ya saki aljihu daidai ƙarfinsa, duk da abin da aka yi mata daga gidansu ya fi wanda ya yi, ya siya tinkiya babba, babanta kuma ya aiko da rago, aka haɗa aka yanka. Wannan shiga jegon da Rauda ta yi shi ya canzawa Ustaz lissafi, ya so ƙwarai ta zauna ta yi wanka a gidansa, amma iyayenta suka ce sai ta tafi gida, shi kuma ba zai iya yin musu da su ba, shi yasa ya haƙura, amma yana cutuwa, haka yake shan juyi a gado kafin bacci ya ɗauke shi, don ma dai kullum sai ya je gidan, kuma yana ɗan taɓa jikinta. A wannan gaɓar ya fara tunanin ya kamata ya ƙara aure tun yanzu, ba dole sai ya jira ya yi kuɗin da yake fata ba, tun da yanzu ma Alhamdulillah yana da halin riƙe mata biyun, don haka ya samu wata ƙanwar abokinsa ya fara kula ta, kuma aka yi sa'a ta amince tana son shi, dama ba a daɗe da fasa aurenta ba, Rauda tana can tana zaman wankan jego, shi kuma yana nan yana soyewa da budurwarsa Zulaiha, sam ba shi da niyyar faɗa mata larurarsa saboda yana ganin ai tun da su biyu ne za a samu sassauci, idan yau ya gajiyar da ita gobe ba ya ɗakinta sai ta huta, a ganinsa duk rakin mace ba za ta yi ƙorafi ba. Rauda ta dawo gidan da sati biyu, Ustaz ya je takanas ya samu mahaifinta da zancen yana sha'awar ƙara aure, ya ɗora da faɗin"Shawara ce dai nake nema, a matsayinka na uba a gare ni Daddy, duk yadda ka ce zan ɗauki shawararka". Daddy ya ce"Malam Ashir ko da ni ne na haife ka ba ni da hurumin saka ko hana ka a fannin ƙara aure, a dai ra'ayina kenan, mai ɗaki shi ya san inda yake yi masa yoyo, idan kana bukatar ƙara aurenka ai ba na jin sai ka yi shawara da wani, abu ɗaya dai shi ne ku tattauna da ita Rauda, idan ta amince Alhamdulillah, idan kuma ba ta amince ba sai a yi abin da ya dace". Ya ce"In sha Allahu ma za ta amince Daddy, kuma ni wallahi ba ta gaza min ba, to kawai dai dama can ina da ra'ayi shi ne yasa". Daddy ya ce"Babu komai Allah Ya zaɓa mafi alkhairi". Suka yi sallama ya tafi, haka ya dinga jinjina yadda zai fuskance ta da batun, ya dai daure ya zaunar da ita ya fara yi mata fira cikin jimami na yadda 'yan mata manya da ƙanana, da zawarawa da iyayen marayu suka yawaita a gari babu aure, babu mashinshini, ya ce"Wato abun akwai ainahin taɓa zuciya, da kuma tausayawa, auren irin waɗan nan matan zai iya zama jihadi mai girma". Rauda sam ba ta fuskanci inda zancen nasa ya dosa ba, ta ce"Hakane, Allah Ya ba su mazaje na gari". Ya ce"Amin". Suka ɗan yi shiru, sannan ya ce"Raudatu". Ta ce"Na'am". Ya ce"Shin za ki iya taimakawa al'umma ta hanyar kwantar da hankalinki idan na auri ɗaya daga cikin waɗan nan matan?" Gabanta ya ba da rass, ta ƙanƙance ido ta ce"Me kake nufi?" Ya ce"Ina nufin na gano wata yarinya, bi ma'ana mun sasanta, in sha Allah zan aure ta". A fusace ta ce"Tabdijan, ai kuwa uban kuturu ma ya yi kaɗan, na rantse da Allah ba zan taɓa zama da kishiya ba har abada, ashe watan rabuwa da ni ya tsaya maka kenan". Ya ce"Ya subhanallah , subhanallah, Rauda ki yi gaggawar faɗin Astagfirullah, domin ina jiye miki azabar Allah, duk da ni fa na yafe miki". A fusace ta ce"Kar ka yafe ɗin, ka daɗe ba ka yafe ba, ma yaudari kawai, ashe maza duka haka kuke? To wallahi ba da ni za a cigaba da wannan zaman ba, dole sai ka sake ni a yau ɗin nan". Ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Rauda don Allah zauna mu fahimci juna kin ji, idan ba kya son ganin ta sai na raba muku gida ma". Ta yi tsaki ta bar falon, ta shiga ɗaki ta saka sakata, haka suka kwana a ɗaki da ban da ban, Ustaz hankalinsa ya tashi, saboda yana son Rauda ko don juriyar da take yi da shi, bai shirya rabuwa da ita ba, uwa-uba yana tsoron kar su rabu ubanta ya ba shi jan kati, shi yasa duk ya firgice. Washegari da sassafe ta haɗa kayanta, lokacin yana bacci ta fice daga gidan, ta ƙarasa gida tana kuka da faɗin sai dai ya sake ta, ran mahaifiyarta ya ɓaci sosai, ta hau faɗa da zagin Ustaz tana ce masa butulu, Daddy ya taka mata burki ya ce ai ƙarin aure ba haramun ba ne, sai dai babu wanda zai yi wa Rauda dole, idan ta ga ba za ta iya zama da kishiya ba to shi zai saka ya sake ta, kuma tun da ba ita ce ta ba shi aiki ba kar ta sake ce masa butulu. Sanda Ustaz ya fahimci Rauda ba ta gidan ba ƙaramin tashi hankalinsa ya yi ba, ko wanka bai tsaya yi ba, ballantana ya nemi abinci, hala ya tafi gidansu da jallabiya, ya durƙusa a gaban Daddy yana ba shi haƙuri, Daddy ya ce"Wannan ba komai ba ne Malam Ashir, tun da ta ce ba za ta iya zaman ba ina ba ka shawara ka sake ta". Ustaz gabansa ya faɗi ya ce"Amma Daddy ba zan so lalacewar alaƙarmu ba, yanzu shikenan sai na daina aiki a ƙarƙashinka ko?" Ya ce"Sam, haka ba zai faru ba, alaƙarka da matarka ce kawai za ta katse, amma batun aiki yanzu ma muka fara, kamar yadda na yi maka alƙawari, wani watan in sha Allah za ka je Cotonou ma, na yarda da amanarka saboda haka idan ka ga na bar aiki da kai to kai ne ka buƙaci hakan". Ya ce"Ba zan ma buƙata ba Daddy, Allah Ya saka da alkhairi". Ya ce"Amin, yanzu yaya kenan? Za ka ba ni takardarta ko kuma a hannunta za ka ba ta?" Ustaz ya ce"Daddy don Allah a yi haƙuri a ba ni lokaci na gana da ita tukunna, in sha Allah zan lallaɓata ta amince". Ya ce"To Allah Ya zaba muku abin da yake alkhairi". Ustaz ya amsa da Amin, ya tashi ya shiga nufi falon. 08028966015 [05/11, 8:20 pm] Sadiya Abdulrazak: 37 Ya daɗe a falon kafin ya samu Rauda ta fito, ya gyara zama ya ce"Sannu da fitowa Hajiyata". Ta ɓata rai ta zauna kamar ba ita ba. Ya ce"Ma sha Allah! To na zo ne dama a kan maganarmu, na yi mamakin yadda kika iya tafiya ba tare da sanina, kin manta hukuncin matar da ta fita ba tare da izinin mijinta ba? Duk taku ɗaya fa da kika yi mala'ilu tsine miki suke yi, idan don ta ni ne na yafe miki, to amma ya za ki yi da hukuncin da Allah Ya tanadarwa macen da ta fita ba tare da izini ba?" Ta ce"Ka faɗi abin da ya kawo ka kawai, tun da ka yafe min sauran tsakanina da mahaliccina ne ai, Allah gafurur rahim ne". Ya ce"Hmm, to la ba'asa, yanzu ya ake ciki? Sulhu khair, Rauda ki nutsu mu yi sulhu". Ta ce"Wallahi ba ka ɗakko hanyar sulhu ba, maslaharka ɗaya ce kawai ka sake ni, ba zan taɓa iya zama da kishiya ba". Ya ce"To ga shi ni kuma ba zan fasa auren da na yi niyya ba, tun da ai taimakon wani jihadi ne". Ta ce"To sai ka sake ni". Ya ce"Ba zan sake ki ba, tun da ni ba butulu ba ne". Ta ce"Ai kuwa wallahi ya zama dole ka sake ni, don ni ba zan zauna da kishiya, kuma ban da butulcin mata nawa ka aura kuka rabu? Kuma na san duk hatijancinka ne ya raba ku, amma ni na jure saboda ina sonka da kuma tausayin aure-auren da kake yi, shi ne za ka ce za ka ƙara aure, to ka je ka yi, la auri wacce kake tunanin za ta iya da kai, ni kam na gama zaman aure da kai". Ta tashi ta bar shi nan zaune, riƙe da haɓa, ya gaji da zama ya tashi ya tafi gida. Tun daga lokacin ta daina amsa kiran shi, kullum sai ya zo amma ƙarshe ma ta daina fitowa falon ballantana ya samu ganinta, sati biyu ana wannan turka-turka, mahaifinta ya zaunar da shi ya ce masa yana roƙon ya saki Rauda, tun da ta ce ba za ta zauna da kishiya ba, shi kuma ba zai fasa auren ba, Ustaz ya diririce tsoronsa ɗaya kar ya ce zai kore shi daga aiki, ya ce"Daddy wallahi ina son Rauda, ba zan iya rabuwa da ita ba". Ya ce"To shikenan, amma za ka yarda da Khul'i ko? Kai malami ne ka fi ni sanin akwai shi, to zan iya ɗaukar wannan matakin, ni ba na son auren dole, zaman aure na mutum biyu ne, tun da ta ce ta gama a bar shi kawai". Ustaz zuciya ta ɗarsa masa idan fa za a yi Khul'in nan ƙila ba ƙananun kuɗi za a ba shi ba, ƙila ma ya samu na auren wata bayan Zulaiha, ya auri mata biyun da yake buri a rana ɗaya, sai kuwa wata zuciyar ya ce bai kamata a yi haka ba, don gudun a kore shi daga aikinsa, ya ce"Daddy kai uba ne a gare ni, ka zaɓa min kawai, duk umarnin da ka ba ni ya zama dole na bi shi nan take". Daddy ya ce"Idan hakane, to ni rabuwarku na zaɓa". Ustaz ya ce"Shikanan, na yi biyayya Daddy, na saki Rauda saki ɗaya amma ba bisa son zuciyata ba". Daddy ya ce"To dama wani abun ai ba dole sai zuciya tana so ba, kuma kar wannan ya saka ka ji kunyata ko kuma ka fara ja baya da ni, alaƙarka da 'yata ce kawai ta zo ƙarshe ba alaƙarka da ni ba, kana nan a matsayin yaron shagona mai amana, wanda nake yaba maka". Ustaz ya ce"Alhamdulillah, na gode sosai, Allah ya saka da alkhairi Ya ƙara girma". Ya koma gida yana jinsa a sanyaye, bai so ya rabu da ita ba, amma Allah Ya ƙaddara sai ya ƙara auren. Yana shan wuya da daddare kafin gari ya waye, da ƙyar yake iya bacci, don haka ya tura neman aure, ya ce wata ɗaya yake so a saka, suka ce sai dai biyu, a dole ya amince, suka cigaba da soyayyarsu, a wannan karon ya fara haɗa lefe, don sun yi magana da iyayenta, ya ce kuɗi zai bayar, suka ce a'a lafe za a yi, gefe guda yana fargabar shin zai cigaba da zama a gidan mahaifin Rauda ne ko kuma zai tashi ungulu ta koma gidanta na tsamiya? Amma yadda ya saba da gidan nan idan aka ce ya tashi gaskiya zai cutu. Akwati huɗu ya yi lefen, ya zuba kaya matsakaita, ba ƙarshen araha ba, ba masu tsada ba, aka kai kaya, aure ya rage sati biyu ya samu mahaifin Rauda da zancen gida, yana sunkuyar da kai ya ce"To Daddy na ce yaya za a yi da batun gidanka da nake ciki? Tun da dai ka ara min ne saboda ita Rauda, yanzu kuma tun da wannan lamari mara daɗi ya faru ban san ya za a ƙare ba, shi ne na ce bari na faɗa maka". Daddy ya ce"Malam Ashir, ka manta da batun Rauda ce ta zama silar haɗuwarmu, a yadda na yarda da kai a yanzu ko ba ka da aure zan iya ara maka gida ka zauna a ciki, babu komai amaryarka ta tare Allah Ya ba da zaman lafiya, kuma ni ina yi maka sha'awar siyan gidan idan kana so, a hankali ka dinga biya har ka gama ya zama naka". Ustaz ya ce"Alhamdulillah ma sha Allah, haƙiƙa Daddy zan so hakan tabbas kai Uba ne a gare ni, na gode sosai Allah Ya saka da alkhairi". Daddy ya ce"Amin, babu komai ai". Ustaz ya dinga kwararawa Daddy addu'a, yan37 Ya daɗe a falon kafin ya samu Rauda ta fito, ya gyara zama ya ce"Sannu da fitowa Hajiyata". Ta ɓata rai ta zauna kamar ba ita ba. Ya ce"Ma sha Allah! To na zo ne dama a kan maganarmu, na yi mamakin yadda kika iya tafiya ba tare da sanina, kin manta hukuncin matar da ta fita ba tare da izinin mijinta ba? Duk taku ɗaya fa da kika yi mala'ilu tsine miki suke yi, idan don ta ni ne na yafe miki, to amma ya za ki yi da hukuncin da Allah Ya tanadarwa macen da ta fita ba tare da izini ba?" Ta ce"Ka faɗi abin da ya kawo ka kawai, tun da ka yafe min sauran tsakanina da mahaliccina ne ai, Allah gafurur rahim ne". Ya ce"Hmm, to la ba'asa, yanzu ya ake ciki? Sulhu khair, Rauda ki nutsu mu yi sulhu". Ta ce"Wallahi ba ka ɗakko hanyar sulhu ba, maslaharka ɗaya ce kawai ka sake ni, ba zan taɓa iya zama da kishiya ba". Ya ce"To ga shi ni kuma ba zan fasa auren da na yi niyya ba, tun da ai taimakon wani jihadi ne". Ta ce"To sai ka sake ni". Ya ce"Ba zan sake ki ba, tun da ni ba butulu ba ne". Ta ce"Ai kuwa wallahi ya zama dole ka sake ni, don ni ba zan zauna da kishiya, kuma ban da butulcin mata nawa ka aura kuka rabu? Kuma na san duk hatijancinka ne ya raba ku, amma ni na jure saboda ina sonka da kuma tausayin aure-auren da kake yi, shi ne za ka ce za ka ƙara aure, to ka je ka yi, la auri wacce kake tunanin za ta iya da kai, ni kam na gama zaman aure da kai". Ta tashi ta bar shi nan zaune, riƙe da haɓa, ya gaji da zama ya tashi ya tafi gida. Tun daga lokacin ta daina amsa kiran shi, kullum sai ya zo amma ƙarshe ma ta daina fitowa falon ballantana ya samu ganinta, sati biyu ana wannan turka-turka, mahaifinta ya zaunar da shi ya ce masa yana roƙon ya saki Rauda, tun da ta ce ba za ta zauna da kishiya ba, shi kuma ba zai fasa auren ba, Ustaz ya diririce tsoronsa ɗaya kar ya ce zai kore shi daga aiki, ya ce"Daddy wallahi ina son Rauda, ba zan iya rabuwa da ita ba". Ya ce"To shikenan, amma za ka yarda da Khul'i ko? Kai malami ne ka fi ni sanin akwai shi, to zan iya ɗaukar wannan matakin, ni ba na son auren dole, zaman aure na mutum biyu ne, tun da ta ce ta gama a bar shi kawai". Ustaz zuciya ta ɗarsa masa idan fa za a yi Khul'in nan ƙila ba ƙananun kuɗi za a ba shi ba, ƙila ma ya samu na auren wata bayan Zulaiha, ya auri mata biyun da yake buri a rana ɗaya, sai kuwa wata zuciyar ya ce bai kamata a yi haka ba, don gudun a kore shi daga aikinsa, ya ce"Daddy kai uba ne a gare ni, ka zaɓa min kawai, duk umarnin da ka ba ni ya zama dole na bi shi nan take". Daddy ya ce"Idan hakane, to ni rabuwarku na zaɓa". Ustaz ya ce"Shikanan, na yi biyayya Daddy, na saki Rauda saki ɗaya amma ba bisa son zuciyata ba". Daddy ya ce"To dama wani abun ai ba dole sai zuciya tana so ba, kuma kar wannan ya saka ka ji kunyata ko kuma ka fara ja baya da ni, alaƙarka da 'yata ce kawai ta zo ƙarshe ba alaƙarka da ni ba, kana nan a matsayin yaron shagona mai amana, wanda nake yaba maka". Ustaz ya ce"Alhamdulillah, na gode sosai, Allah ya saka da alkhairi Ya ƙara girma". Ya koma gida yana jinsa a sanyaye, bai so ya rabu da ita ba, amma Allah Ya ƙaddara sai ya ƙara auren. Yana shan wuya da daddare kafin gari ya waye, da ƙyar yake iya bacci, don haka ya tura neman aure, ya ce wata ɗaya yake so a saka, suka ce sai dai biyu, a dole ya amince, suka cigaba da soyayyarsu, a wannan karon ya fara haɗa lefe, don sun yi magana da iyayenta, ya ce kuɗi zai bayar, suka ce a'a lafe za a yi, gefe guda yana fargabar shin zai cigaba da zama a gidan mahaifin Rauda ne ko kuma zai tashi ungulu ta koma gidanta na tsamiya? Amma yadda ya saba da gidan nan idan aka ce ya tashi gaskiya zai cutu. Akwati huɗu ya yi lefen, ya zuba kaya matsakaita, ba ƙarshen araha ba, ba masu tsada ba, aka kai kaya, aure ya rage sati biyu ya samu mahaifin Rauda da zancen gida, yana sunkuyar da kai ya ce"To Daddy na ce yaya za a yi da batun gidanka da nake ciki? Tun da dai ka ara min ne saboda ita Rauda, yanzu kuma tun da wannan lamari mara daɗi ya faru ban san ya za a ƙare ba, shi ne na ce bari na faɗa maka". Daddy ya ce"Malam Ashir, ka manta da batun Rauda ce ta zama silar haɗuwarmu, a yadda na yarda da kai a yanzu ko ba ka da aure zan iya ara maka gida ka zauna a ciki, babu komai amaryarka ta tare Allah Ya ba da zaman lafiya, kuma ni ina yi maka sha'awar siyan gidan idan kana so, a hankali ka dinga biya har ka gama ya zama naka". Ustaz ya ce"Alhamdulillah ma sha Allah, haƙiƙa Daddy zan so hakan tabbas kai Uba ne a gare ni, na gode sosai Allah Ya saka da alkhairi". Daddy ya ce"Amin, babu komai ai" Takanas ya saka shi a addu'a a wannan daren, yana mamakin irin zuciyar shi, bai faɗaqa Zulaiha shi hariji ba ne, saboda ya yi alƙawin zai rage, ba zai takurata sosai ba, sannan sati ɗaya da auren ma ya kama zai tafi Cotonou, da ranar ta zo aka ɗaura auren Ustaz a karo na huɗu, yana ta farincikin yau zai sauke nauyin da ya jima bai sauke ba, bayan an kawo amarya kowa ya watse suka shiga firar farinciki ana cin kaza, ita ma yarinyar tana son shi, don haka ta so ta saki jiki a wannan daren ta ba shi farinciki, amma Ustaz sai da ya ƙaryata jarumtarta, don tun yana lallaɓawa yana binta a hankali har dai ya manta da amarya yake tare, don haka sosai ya jigata ta, kuma da asuba ma duk yadda ya so daurewa kasawa ya yi sai da ya ƙara nemanta, da rana ma kafin a fara yin baƙi ya yi, ai kuwa cikin wuni ɗaya yarinya ta firgice ta yi zuru-zuru, idanunta sun kumbura, ga wani tsoron shi da ya shiga zuciyarta, ta yi kuka babu adadi kafin la'asar 'yan'uwanta su zo. Suna ganinta a haka suka san abin da ya faru, amma a zaton su raki ne kawai ya saka ta wannan firgicin, da suka tambaye ta ta fashe da kuka tana cewa"Ba zan iya ba Anti, wallahi kashe ni zai yi". Yayar tata ta fara dariya tana tuna yadda Zulaiha ta dinga rawar kai da aka haɗa mata magunguna, na sanyi sai da ƙyar take sha, amma daka da tsumi haka ta dinga sha babu ko jin kunya, shi ne a kwana ɗaya za ta karaya? Suka dinga kwantar mata da hankali da faɗin za ta saba, kowa ma a haka ya saba, haka suka tafi suka bar ta bayan sun yi mata girkin dare, ta dinga jin kamar ta bi su. A daren ma Ustaz bai tausaya mata ba, saboda ko ya ce zai rabu da ita, sai ya ƙi kamar mayen ƙarfe yana jan shi, dole ba zai iya jurewa ba, a ranar ta uku kuwa dare yana yi ta rufe ƙofa, duk wa'azin shi da magiya, tare da alƙawarin yau ba zai yi mata komai ba ta ƙi buɗewa, haka ya haƙura, daga ranar ba ta sake yarda da shi ba, sai ana gobe zai yi tafiya ya samu nasarar dirtse ta da rana ya yi ta ƙarfi, ai kuwa washegari yana tafiya ta haɗa kaya ta tafi gidansu, a ƙa'ida kuma cewa aka yi kakarta, za ta zo su zauna, ai kuwa ta koma gida tana ta kuka, ta ce ita fa na za ta koma ba sai dai ya sake ta, kuma tambayar duniyar nan ta ƙi faɗar dalili, aka tambaye shi ta waya shi ma ya ce bai san dalili ba, a dole aka bar batun ana jira ya dawo a tattauna. SAYYADA A hankali na saba da rashin fita waje, da kuma rashin Saddam, ba don na manta da shi a zuciyata ba, kuma soyayyar shi tana nan daram, sai dai kawai na danne, har na yaye ɗana yana wata goma sha shida babu wanda ya zo ya ce yana sona, to wa ma ya san ba ni da aure ban da 'yan cikin unguwarmu? Tun da ba fita nake yi ba, ban ga ta inda zan haɗu da wani har ya ce yana sona ba, kuma ni hakan daɗi yake yi min sosai. Ana haka ne wataran kawai Baba ya ce min yau zan yi baƙo, gabana ya faɗi na ce"Baba baƙo kuma?" Ya ce "E baƙo, magidanci ne mai hankali, ya zo sati biyu da suka wuce mun yi magana da shi, kuma na fahimci aurensa ne ya dace da ke, matarsa ba ta haihuwa shi ne yake so ya ƙara aure, ba shi da wata matsala, don 'yar'uwarki Anisa ce ta ba shi labarinki, Ogan mijinta ne a wajen aiki, ya ba shi cigiyar ya samo masa mace mai hankali, shi ne yake bawa Anisan labari dayake tana sonki da arziƙi sai ta ce ga ki nan, yanzu haka ya ga hotonki kuma ya ce kin yi, saboda haka yau zai zo ku gana, ina fatan ba za ki yi abin da za ki kunyata ni ba ko?" Na jinjina kai alamar e, wani abu ya taso ya tokare min ƙirji, ko zan yi hasashen ga ni na yi aure da Sadam kawai nake hangowa a gidanmu da muka yi rayuwa, ta ina zan fara rayuwa da wani ba shi ba? Kuma wai ma yana da wata matar, sannan auran ma don yana son haihuwa ne zai yi, kenan ma abin da zan haifa zai so ba ni ba, na share hawaye da ya sakko min. Har ji na yi kamar zazzaɓi zai kama ni, da yamma ya zo, zan fita Mama ta ce min"Sayyada a matsayina na mahaifiyarki ina ba ki shawarar ki saurari mutumin nan ki ba shi dama, a kan Sadam kike yin komai, kuma ni da mahaifinki mun lashi takobin ba za ki aure shi, don haka ki bawa wannan ɗin dama". Na ce"To" A sanyaye na fita. Na yi zaton zan ga irin ɗirka-ɗirkan mazan nan masu ƙiba, sai na ga saɓanin haka, ba dai siriri ba ne, amma ba za a kira shi da lukuti ba, ban ma wani ƙare masa kallo ba ballantana na gano muninsa ko kyau, na yi sallama, ya amsa, na yi shiru ina jira na ji ta inda zai fara, dai ji na yi ya ce"Ke ba ki iya gaisuwa ba ne?" Na ce"Ita ka zo ji?" Ya yi shiru na 'yan sakanni kafin ya ce"A'a, ganinki na zo, kuma na ganki kin yi, duk da ba ki da kunya, amma ki kwantar da hankalinki in sha Allah zan aure ki a hakan, to ni fa? Na yi miki?" Na ce"Ba ka yi min ba, kuma ba za ka taɓa yi min ba, sannan rashin kunya kaɗan ma ka gani". Ya jinjina kai ya ce"Na yi ko ban yi ba wannan ba zai zama damuwa ba, tun da dai mahaifinki ya ce ya ba ni ke, kuma na ga kin yi min, to ki kwantar da hankalinki in sha Allah za a yi auren, kuma shi ma rashin kunya da kike ji da shi, ki kwantar da hankali zan sauke miki shi da izinin Allah". Na ce"Idan ka gama zan tafi". Ya ce"Babu damuwa, na lura ba kya sona, amma ki kwantar da hankalinki ni ban damu sai kin so ni ba, indai za ki dinga bari na yi amfani da ke a matsayinki na matata to babu damuwa". "Amfani?" Na maimaita kalmar a zuciyata, wannan anya kuwa ba ɗan iska suka turo min ba? Ya ce"Ki je gida ki kwantar da hankalinki, na cewa Baba ya ba ki wayarki, amma ya ce ba zai yiwu ba sai bayan aure, don haka zai iya kiranki a wayar Mama a kowane lokaci, sai ki tara, sai anjima, na bar ko lafiya". Na daskare a tsaye ina bin shi da kallo, har wanda yake tsaye a jikin motar ya buɗe masa ya shiga suka ja suka tafi, baƙinciki ya yiwa zuciyata ƙawanya, na ƙara jin tsanar Anisata taso min, na shiga gidan, na fashe da kuka na yi ɗakina. 08028966015 [06/11, 5:05 pm] Sadiya Abdulrazak: 38 Na zauna na ci kukana, ina tunanin Anisa tana sane ta kawo min wannan ɗan iskan, mara mutunci, da Baba ya dawo ya kira ni, ya ce"Sayyada baƙonki ya zo, kin gan shi, ya yi miki ko bai yi ba?" Da sauri na ce"Bai yi ba". Baba ya ce"Mene ne matsalar shi". Na ce"Kawai bai yi min ba". Ya ce"To ai kuwa dole sai kin samo matsalar shi kafin a sallame shi". Na rushe da kuka ina so na faɗa musu ni duk wanda ba Saddam ba ba zai yi min ba, amma babu dama, na dinga kuka ina jin ƙuncin zuciyata yana raguwa silar kukan, a halin da nake ciki kafaɗar da zan kwanta na yi kukan nake nema, amma babu idan ba ta ɗana ba, kukana ta taɓa zuciyar Mama, da alama ta fara tausayina, a sanyaye ta ce"Sayyada ya isa haka, ba fa son ki ne ba a yi ba, ke ce kika ja komai, kin yi abubuwan da dole za mu zarge ki ko da matar Saddam ƙarya ta zo ta faɗa mana, idan 'yar da kika haifa ce aka ɗarsa miki zargin tana aikata zina wane irin mataki za ki ɗauka? Ki yi wa kanki adalci mana, dole za a karɓu wayarki tun da ba kya jin magana, dole za a hana ki fita saboda kina taurin kai, idan aka bar ki ki fita ba za ki haƙura da Sadam ba, sannan tun da kin saba da aure ba za ki juri dogon zaman zawarci, shi yasa muke so ki auri wani". Cikin kukan na ce"To don Allah kar ku yi min auren dole, ba na son mutumin nan". Baba ya ce"Sayyada, na ji kokenki ba kya son auren dole ko? To zan dakatar da shi in sha Allah! Sai dai na ba ki wata ɗaya ki fitar da wanda za ki aura, amma ban da Sadam". Mama ta ce"Yawwa, kin ga kin samu sassauci, wannan shi ne adalcin da za mu iya yi miki, ki samo wanda kike so ki kawo, ban da Sadam". Gani nake idan zan kewaye duniya ina duba maza da halayensu ba wanda zai yi min sai Saddam ɗin da ba sa so, amma sanin ba ni damar furtawa sai na ce"Baba ta ina wani zai gan ni ya ce yana sona? Ba fa na fita ko ƙofar gida, sannan a wancen karon haka suka dinga zuwa suna fasa auren, ba na so wannan karon ma ya faru". Ya ce"To wannan kuma ke ta shafa, tun da dai ke ce kika ja wa kanki abin da za a fasa ɗin ai, yanzu na janye takunkumin fitar taki, na tsayin wata ɗaya, sannan za a ba ki wayarki". Na ji wani daɗi ya ratsa ni. Ya ɗora da faɗin"Sai dai kuma, idan na samu labarin kina waya da yaron nan Saddam, ko kuma kun haɗu da shi ko sai ɗaya ne, to ki sani kina da zaɓi biyu a lokacin, ko dai na aura miki wanda na so a ranar, ko kuma na zare hannu a lamarinki ki bar min gida bari na har abada don ni ba ƙaramin yaro ba ne da za ki dinga raba min hankali". Na jinjina kai, alamar na yarda amma a zuciyata ban yarda ba, Mama ta shiga ɗaki ta ɗakko min wayoyin ta ba ni, na karɓa jikina yana rawa, sai tsakar dare aka kawo wuta, amma haka na bi daren na saka caji, na kunna ta wajen Sadam, na yi mamakin ganin babu saƙon shi, dama whatsApp tuni ya yi expire, na saka kati ta bankina na sayi data, na sauke whatsApp ɗin, na nemi lambar shi, na yi masa sallama, don ma dare ne na san yana bacci da kiran shi zan yi. Ai kuwa da asuba ina idar da sallah na kunna data, ban daɗe a online ɗin ba na ga ya ƙi hawa, kawai na kira shi, tun da na san ai ba shi da aure ba laifi ba ne idan na kira shi, ya ɗauka da sallama, na amsa na ce"Ka tashi lafiya?" Ya ce"Lafiya ƙalau". Na ce"Sadam, na yi kewarka sosai". A takaice ya ce"Ok". Jikina ya fara yin sanyi na ce"Amma ba ka yi kewata ba ko? Na ga kamar babu shauƙi ko zumuɗi a muryarka". Ya ce"To so kike na kashe kaina saboda ke? Sayyada ba kya sona, shi yasa kika karɓu hukuncin da iyayenki suka yanke a kan soyayyarmu, wallahi ni kin ba ni mamaki matuƙa". Kamar zan yi kuka na ce"To ya zan yi? Iyaye ne, sannan sun toshe duk wata kafa da za ta sada ni da kai, ba na son yawan saɓa musu a yanzu aljannata a ƙarƙashin ƙafarsu take, don Allah ka fahimce ni". Ya ce"Fahimta ai na gama tun da kika nuna min ba ki damu da ni ba, sannan kar ki sake kirana a daidai wannan lokacin". Na ce"Me yasa?" Ya ce"Saboda na yi aure, hakan zai sosa ran matata, yanzun ma falo na fito nake ɗaga wayar". Kalmar 'Na yi aure' ta shiga amsa kuwwa a kunnena, fitar numfashina ya canza nan take, na ce"Ka yi me ka ce?" Ya ce"Na yi aure, na auri wacce take sona, yanzu haka ma tana da cikin wata biyu, zai fi miki kyau ki je ki cigaba da bin umarnin iyayenki". Wani irin ƙunci ya mamaye ni, duk yadda zan faɗi halin da na shiga na ɓacin rai ba za ku gane ba, nan take ya sire min a raina, na ce"In sha Allah zan yi musu biyayya, ba zan tozarta ba kuma albarkacin biyayyar da zan yi, kai guba ne a gare ni Saddam, ba zan taɓa yafe maka ba". Na yi jifa da wayar na fashe da kuka mai sauti, wanda ya ankarar da Mama akwai matsala, don tana tsakar gida tana haɗa wutar da za ta dafawa Baba ruwan zafi, zai yi sammakon fita. Ta shigo ɗakin da sauri tana tambayata "Sayyada lafiya? Mene ne?" Na kasa magana sai kuka, sai da ta fara zagina sannan na ce mata"Babu komai". Ta ce"Kin ci gidanku, to hauka kika fara yi da za ki dinga wannan kukan kuma ki ce babu komai?" Sai ga Baba ma ya zo yana tambayar me aka yi min. Na ce"Wallahi babu komai, kawai dai na gane na yi kuskure, ku yafe min don Allah, Baba ba sai na fara fita na jira wani ya ce yana sona ba, ko wane ne ma indai ya yi maka ina son shi, a yi auren kawai fatana dai ku yafe min". Baba ya ce"Sayyada na yafe miki, Allah Ya shirye ki, Ya shiga lamarinki, Ya tseratar da ke daga kaidin namiji, Allah Ya ba ki miji na gari". Ya juya ya bar ɗakin. Mama kuma ta zauna ta saka ni a gaba da tambayar me ya saka ni kuka? Na ce"Kawai tunani na yi Mama, ban kyauta muku ba, shi ne na saka a raina zan cire son Sadam daga zuciyata, shi ne kawai abin da ya saka ni kuka". Mama ta ce"Sayyada na san kina son shi, na san rabuwa da abin da kake so akwai zafi, amma ki gane shi ba sonki yake yi ba, ke ce kike son shi, zai wahalar da ke, saboda kin ba shi kofofi da dama wanda zai taka ki yadda yake so idan ya aure ki, wannan tozarcin nake guje miki, ina so rayuwarki ta inganta ne, yanzu zan roƙi mahaifinki ya ƙara miki lokaci zuwa wata uku, ko Allah zai kawo wani wanda kike so, tun da kin ce wannan ɗin bai yi miki ba". Na ce"Mama ai a yau na buɗe ƙofar zuciyata duka, zan karɓi duk wanda kuka zaɓa min in sha Allah, ko an ba ni lokaci babu wanda zan kawo a matsayin ina son shi, amma zan yi aure, saboda kuna so, kuma ibada ne, domin na gama so!". Jikin Mama ya yi sanyi, ni kuma na share hawayena, a daidai wannan lokacin na saka a raina ba zan sake kuka saboda Sadam ba, ba ma shi kaɗai ba, babu wani namiji da zan bari ya ƙara saka ni kuka wai saboda ina son shi, na yi alƙawari da zuciyata zan rabu da shi har abada, don haka na tashi na bar Mama a zaune, na fita na kunna mata wutar, kafin azhar na warware na saki jiki sosai, amma idan ka yi min kallon nazari ba na fuskata ba za ka gane ƙarfin hali kawai nake yi, da son ɓoye jinyar dake cikin zuciyata, na cigaba da ƙarfafa kaina saboda na san ta hakan zan manta da shi har abada. Da daddare Mama take cewa Baba tun da na amince ai sai a yi a wuce wajen, ya ce a'a, ya riga ya dakatar da shi, kuma wata uku ya ce masa, a bar ni na huta tukunna. Bayan kwana uku sai Sadam ya kira ni, ban ɗauka ba, sai ma block dinsa da na yi ta ko'ina, kuma na goge lambarsa. Haka na fara gudanar da wata rayuwa mai cike da son ƙarfafawa kaina gwiwa, a hankali mu fara dawowa kamar da ni da Mama da ma sauran 'yan'uwa, na fara zuwa sabga, biki ko suna ko dubiya, idan na so sabunta iska ma haka kawai nake kai wa 'yan'uwa ziyara, amma sam ban da Anisa. USTAZ Sati biyu ya yi ya dawo, a jigace ya dawo, kawai son kasancewa da matarsa yake, ya yi takaicin rashin zamanta a gidan, haka ya yi wanka ya tafi gidansu da yamma, rarrashin duniyar nan ya yi mata tare da alƙawarin zai rage, amma sam ta ce ba ta yarda ba, ita ba za ta koma ba, Allah Ya taimake ta iyayenta ba masu tirsasawa yarinya ba ne, don haka suka tambayi Ustaz ya faɗa musu me ya haɗa su tsakanin shi da Allah, kunya duk ta kama shi, ya fara bayani"To Baba a gaskiya ba zan ɓoye maka ba, ina da wani laruri, bi ma'ana ni hariji ne, wannan shi ne, ita kuma Zulaihat ta kasa jurewa". Babanta ya ce"Dama ya za a yi ta jure? Ai mu idan haka ne ka yaudare mu, tsakani da Allah ba ka kyauta mana ba, kana Malami kake irin wannan munafurci?" Ustaz ya ce"A yi haƙuri Baba, in sha Allah zan gyara, zan rage lamarin, duk da dai halittar ce a haka, amma zan yi iya ƙoƙarina na rage". Baban ya ce"A'a babu wannan maganar, ba zai yiwu ba, ni dai ba zan yi mata tilas ta koma ga halaka ba, Zulaiha tana da hakuri, tun da ta kasa jurewa to fa an kai maƙura ne, don haka tun da ta ce ba za ta koma ba ka sallame ta kawai". Ustaz ya ce"Subhanallah, Baba saki fa ba abu ne mai sauƙi ba, shi ne halal ɗin da Allah ba ya so". Baba ya ce"Tun da aka halatta ai ba haramun ba ne, kuma an yi shi ne don an san dama irin haka za ta faru, wanda saki ne zai zama maslaha, don haka ka sallame ta ɗin kawai". Ustaz ya duba ya ga kuɗin da ya kashe, ya tuna yadda ya dinga ba da kuɗi ana haɗa lefen nan, kuma a ce wai ya sake ta? Kwana uku ne fa kawai ya mori kuɗinsa, ya ce"Kai, ina! Baba a ba ni lokaci zan yi shawara da tunani". Suka rabu a kan haka, Baban yana jin ko auren kwana ɗaya ne ya yarda ya mutu a ce mata bazawara da dai ta yi zamam auren da za ta cutu. Ustaz ya koma gida jiki a mace, haka ya buɗe babin kewar mace a kusa da shi, sai ya fara azumi idan ya yi yau gobe ya huta, sannan da abun ya bijiro masa zai ɗauki Qur'ani ya fara karantawa, da daddare ne dai dole sai ya yi istimna'i yake iya bacci, abun yana damun shi sosai, sai da ya yi watanni biyu a haka, a wata na ukun suka nemi ya sake ta ko su yi ƙarar shi, haka ya sake ta ba don ran shi ya so ba, ya rasa yadda zai yi, yana buƙatar auren kuma shi zuwa yanzu ya fara karaya, yana tsoron sai ya gama kashe kuɗinsa ya sake auro gaibu, don haka zuciya ta ba shi shawarar kawai ya komawa Rauda su sasanta, ai dama don zai yi aure ne, yanzu kuwa tun da babu auren za ta yarda ta dawo. Da wannan tunanin ya shirya ya je gidan su Rauda, tun a farfajiyar gidan zuciyarsa ta tsinke, sakamakon ganinta da ya yi tana zance da wani babban mutum, ya zauna cikin ɓacin rai sai da ta gama mutumin ya tafi sannan ya tsayar da ita, ya daure suka gaisa, ya ce"Rauda wannan wane ne?" Ta ce"Tsohon saurayina ne, kuma wanda zan aura yanzu in sha Allah, a baya ya so ƙwarai ya aure ni, amma soyayyar ka ta rufe min ido, yanzu kuma idona ya buɗe". Ya ce"Amma za ki ce wannan sangamemen mutumin ba shi da aure, ko kuwa kishiyar ta gidana ce ba za ki iya zama da ita ba?" Ta ce"Ƙwarai kuwa ba shi da aure, ya yi aure amma yanzu sun rabu da matar, don haka zan aure shi in sha Allah, nan da sati uku". Wani abu ya daki zuciyar Ustaz ya ce"Ban gane sati uku ba, me kike nufi kenan? Kina nufin za ki tsige yarona daga nono ba tare da kin yaye shi ba saboda za ki yi aure?" Ta ce"Babu dalilin yaye shi lokaci bai yi ba". Ya ce"Kina nufin da ɗana za ki tafi gidan wani zindiƙi alhalin kina shayarwa? Ɗana ya sha abun nan, shi ma ya sha? To haram, muddin kika tafi ɗana wallahi na haramta miki ki ba shi abin nan ya sha, har sai kin yaye ɗana, wannan wane irin kwaɗo ne? Saurin me kuke yi da ba za ki bari ki yaye shi ba?" Ta ce"To idan kana da iko ka yanke abun ka haɗa da ɗan ka tafi da shi, tun da dai ka fi ni iko da jikina, aure babu fashi, nan da sati uku in sha Allah". Hankalin Ustaz ya tashi sosai, ya ce"Kin ga Rauda mu bar wanann sa'insar, ni fa yanzu bazawari ne, na saki ita amaryar saboda ke, bi ma'ana na gano ke nake so na ke ba, na gaji fa kewarki, don haka a yi haƙuri ki dakatar da wannan aure mara fa'ida, mu mayar da aurenmu a gobe ma, ina da sadakin da zan ba ki in sha Allah!". Rauda ta ce"Ai ka riga ka makara, ka ɓarar da damarka, na gama aurenka in sha Allah, sai sabon miji, sabuwar rayuwa". Daga haka ta shige gidan ta bar shi tsaye yana salati. 08028966015 [08/11, 7:15 pm] Sadiya Abdulrazak: 39 Ustaz fa ya shiga tashin hankali, sai yanzu ya gane ma ashe sosai yake son Rauda, kuma idan ya rabu da ita ya tafka babbar asara, tun da har ta iya zaman da ta saba da shi da larurar shi ai ba ta cancanci haka daga gare shi ba, da a ce ya san wacce zai aura ba za ta iya sabawa da shi ba, da zai zaɓi ya fasa auren a kan dai ya kashe kuɗinsa kuma ya saki wacce take iyawa da shi, ya so ya tunkari mahaifinta da maganar amma kunya ta hana shi, da ya tuna duk irin halakcin da mutumin ya yi masa amma ya shafawa idanunsa toka ya sakar masa 'ya, ya matsawa Rauda da waya yana roƙonta ƙarshe ma sai ta yi blocking ɗinsa, tun daga ranar kullum sai ya je, duk da ba fita take ba, wataran Daddy ya rufe ido ya taka masa burki da cewar tun da ta ce ba za ta koma ba ya rabu da ita, daga nan ya haƙura ya saddaƙar, ya rungumi ibada da kasuwancin shi. Allah Ya taimake shi ranar ɗaurin Rauda ba ya garin, Daddy ya aike shi wata tafiya ta sati ɗaya, amma da ya zai ji a ce ya je ɗaurin aurenta? Kuma ba zai iya ƙin zuwa ba saboda yi wa Daddyn kara, kuma yana takaicin wai a ce an rasa me tsawatar mata, da ɗan shi za ta tafi gidan wani ƙato ko yaye shi ba ta yi ba. Rauda amarya ana ta rawar kai da ta jiki an yi sabon aure, tabbas tana son Ustaz, amma tun da ya iya zaɓar rabuwa da ita a kan ƙarin aure ya fita daga ranta, ta dinga ƙoƙarin mantawa da shi, za a iya cewa ta yi nasarar cire son shi daga zuciyarta da kaso tamanin cikin ɗari, amma fa tun kafin wata ɗaya da mutuwar auren gangar jikinta ta fara kewar shi, dama can ya lafiyar kura ballantana ta yi hauka? Tun tana buduruwa take fama da yawan jin sha'awa ballantana yanzu da ta yi auren, kuma ta gamu da miji irin Ustaz, kuma a ce yanzu za ta yi sabuwar rayuwar da babu namiji? Haka ta dinga daurewa, shi yasa tana gama idda ta fara kula mazan da suka samu labarin mutuwar aurenta, a ciki kuma ta zaɓi tsohon saurayinta Habibu, domin ta yarda da soyayyar da yake yi mata. Tana kewar kashe arna, don haka ta yi gyara sosai, ta kashe kuɗi kamar za ta koma buduruwa, bayan 'yan kai amarya sun watse tana zaune a falo da ɗanta, wanda bai kai ga yin bacci ba, saboda ya yi na yamma, tana ta yi masa wasa, ango ya shigo cike da zumuɗi, amma sai ta ga karsashin na shi ya ragu, ya nemi waje ya zauna a kusa da ita yana faɗin"Ranki ya daɗe amaryata". Ta ce"Sannu da zuwa". Ya kalli yaron, sai haushin shi ya kama shi, saboda ya rage masa jin daɗi, ba don da shi ba da yanzu ya rungume ta, ko ita ta zo ta tare shi tun kafin ma ya zauna, ƙila ma da a rufe zai zo ya tarar da fuskarta, ya buɗe mata kamar buduruwar amarya, amma wannan yaro ya canza lissafin, dama har ran shi ba wai son yaron ne ya sa shi cewa ya yarda a yi auren ba, kawai ita yake so, kuma ya gaji da zaman gwauranci shi ma yana so ya yi aure, da ma tsoron ya bari ya huce lokacin da za ta yaye ɗan kuma wani ya canza mata tunani, amma a gaskiya zai rage masa jin daɗi. Ya sauke numfashi ya ce"Ɗan naki bai yi bacci ba ne?" Ta ji kalmar ɗan naki babu daɗi, ko babu komai ai ya kamata ya yi mata kara, ta maze ta ce"E tukuna dai". Ya ce"To ai shikenan, amma dai da kin ajiye shi mun yi sallah, mun yi abin da yake gabanmu ko?" Ta ɗan yi jim kafin ta ce"Bari na goya shi". Ya ce"A haba wane irin goyo? Ajiye shi don Allah". Ta ce"Da na goya shi ɗin ai bacci zai yi". Ya tashi ya yi gaba zuwa ɗakinsa yana cewa"To shikenan idan ya yi baccin kya ƙaraso, ina jiranki". Duk sai jikinta ya yi sanyi, don ta saka ran nuna soyayya da rawar ƙafa sosai a daren farkonta da Habibu, sai ta ga saɓanin haka. Ba ta gama tsinkewa ba sai da ya yi baccin ta je ta kwantar da shi a nata ɗakin, ta sake yin wanka ta yi alwala ta ɗora hijjabi a kan rigar baccin, ta kwashi kayan ciye-ciye da ya dawo da su ta juye ta nufi ɗakin nashi, yana zaune yana danna waya, ta shiga da sallama, ya amsa yana murmushi ya ce"Masoyiya ya yi baccin?" Ta ce"Ya yi". Ya ce"To Allah Ya sa dai ba ya farkawar dare, don gaskiya ba zan so a ce ki dinga katse mana jin faɗi ba idan ya farka". Ta yi murmushin yaƙe ta ce"Ai kuwa yaro mai shan nono ba a raba shi da farkawar dare". Ya ce"To a gaskiya ina ga za a ɗaukar masa mai raino ta dinga kwana da shi, idan ya farka ta ba shi madara, wannan duka zan ɗauki nauyi, kawai saboda na samu kasancewa da ke tun daga farkon dare har ƙarshe". Rauda ta yi jimm, sannan ta ce"Amma kuma ga ni da raina da lafiyata, sannan hidimar gidan ba yawa ta yi min a ce a ɗaukarwa yarona mai raino kuma a na ba shi madara?" Ya ce"To ya kike so a yi kenan idan ba haka ba Rauda? Ai na faɗa miki uzurina". Ta ce"Na ji uzurinka, amma a matsayina na uwa, uwar ma me haihuwar farko zan ɗauki uzurinka a matsayin mai rauni, na yi maka alƙawarin za mu dinga kwana tare, amma zan dinga zuwa ina duba halin da ɗana yake ciki dole, kuma ba na bukatar sirka masa shayawar da madara, ka yi min wannan alfarmar". Ba don ya so ba ya ce"To shikenan". Suka yi sallah, suka yi ciye-ciyensu, har alla-alla yake a gama su kwanta, yana ta nuna zalamarsa, wanda hakan yake farantawa Rauda, tana jin yau za ta sauke nauyin dake tare da ita tun mutuwar aurenta. Da fari kamar za a yi abun arziƙi, amma sai dai me? Ana shiga fagen dagar komai ya kuncewa Rauda, wannan abu da ya faru a daren yau ta iya cewa an lasa mata zuma ne a baki an janye, saboda sanda ta fara ɗaukar saiti shi kuma lokacin ya samu cikakkiyar gamsuwar shi, ya matsa gefe, gabanta ya faɗi, sosai ta shiga damuwa, don ita ko ɗakko hanya ma ba ta yi ba, ta so ta kalli agogo kafin farawar, amma duk da ba ta kalla ba ta san a ƙiyasi ba zai wuce minti goma ba, tana ta wannan saƙa da warwara har ya yi wanka, ya dawo ya rungume ta yana tambayarta ba za ta yi wanka ba sai da asuba? Kamar ta ce masa bai ishe ta ya taimake ta ya ɗan ƙara, amma ta zame a sanyaye ta sauka daga gadon, ta shiga wankan, bayan ta gama kafin ta kwanta sai da ta je ta duba ɗanta, ta dawo ta kwanta, ya rungume ta yana yi mata firar soyayya, hakan ya sa ta ji kamar susa yake yi mata a saboda halin da take ciki, tana jin lokacin da ya yi bacci, ita kuwa ta kasa yi da ƙyar ta samu ta ɗauke ta. Tana jiyo kukan ɗanta ta zame ta tafi, a nan ta ƙarasa baccinta. Washegari da asuba ta yi zaton zai ƙara yi mata ko minti goman ne, amma sai ta ga babu alama, haka da rana a gidan ya wuni amma sai dai ya yi ta taɓa ta, wancen babban lamarin dai babu shi, duk da yana ta yi masa sambatun daren jiyan, sai dare, yau kam da wuri yaro ya yi bacci, don haka tun farkon dare aka fara kashe arnan, wata zuciyar tana ta faɗa mata jiya gajiyar ɗaurin aure ce ta sa shi rashin nisan zango, yau zai ba ta mamaki, amma me? Sai ga shi irin na jiyan dai, a ranta ta ce'Na shiga uku ni Rauda, a haka rayuwar za ta tafi?' Da haka rayuwar ta fara, tun da aka yi auren Rauda ba ta samu cikakkiyar nutsuwa ba, kuma a hakan ma bayan an gama cin amarci sai ya zamana ba kullum ake yi ba ma, idan an yi yau gobe babu, tun tana daurewa har ta fara nunawa, da ta ga za ta cuci kanta sai ta fara bayyana masa, idan ya gama samawa kansa nutsuwa sai ta ce bai ishe ta ba, sai dai duk yadda ya so ya koma second round ba ya iyawa, sai dai ya yi ta jagwalgwalata har ta ɗan rage, ba don ta gamsu ba, a hankalin kuma ta fara sabar masa da ita fa kullum take so, tun yana daurewa yana biye mata, har ya fara nuna gajiyawarsa, tana ta tsiro da dabarun jan hankalinsa, ta yi shiga ta ɗaukar hankali, amma wataran duk da haka dai ya ce mata yau a gajiye yake, ko kuma bacci yake yi, sai ta raba dare cikin takaici, akwai ranar da ta fara lalubar shi, ya janye hannunta yana cewa "Wai ke Rauda wace irin jarababbiya ce? Wallahi da buduruwa na aure ki da babu abin da zai hana ni zargin ba ta kaina kika fara sanin namiji ba, kai shi yasa ma auren wata bazawarar matsala ne, ke kuwa tsohon mijinki wane iri ne haka? Amma dai ya yi miki banzan sabo". Maganar ta yi wa Rauda zafi sosai, daga ranar ba ta sake neman shi ba, idan ya neme ta shikenan idan bai nema ba ta haƙura, ƙarshe ma sai ta bar masa ɗakin, ta koma kwana da ɗanta, sai dai ranar da ya buƙace ta ya kira ta. Ai kuwa cikin lokaci ƙanƙani soyayyarsa ta dinga malalewa daga zuciyarta, musamman da yake nuna bai damu da ɗanta ba a fili, zuwa lokacin ta riga ta yi nadamar auren shi, ta fara tunanin da zai sake ta babu abin da zai hana ta komawa gidan Ustaz ko da ma zai yi mata kishiyar. SAYYADA Da lokacin da Baba ya ɗibar min ya yi, sai ya zaunar da ni cikin lumana yake ce min"Sayyada watanni uku cika cikin hukuncin Allah, an ba ki wayarki, sannan kina ta fita duk inda kika so, a cikin watannin nan kin haɗu da wanda kuka fara soyayya?" Na ce"Baba ban haɗu da kowa ba". Ya ce"To kina so a ƙara miki lokaci ne ko kuma za ki karɓi shi wannan mutumin da na dakatar da shi?" Na ce"E ba shi dama Baba". Ya ce"To shikenan Allah Ya yi miki albarka, zan sanar da shi in sha Allah". Washegari sai ga kiran waya da baƙuwar lamba, na ɗauka muka gaisa ina son tuna inda na san muryar, ya ce"Kin gane ni kuwa? Isma'il ne, manemin aurenki". Na ce"Ok". Ya ce"Na karɓi lambarki ne dama, don na faɗa miki zan shigo yau, kuma mu dinga gaisawa ko?" Na ce"Allah Ya kai mu". Ya ce"Ok, to ya garin?" Na ce"Ƙalau". Ya ce"To sai na zo". Ban amsa ba na katse kiran, na zauna jigum, ina tunanin yadda rayuwa take yi da ni. Da yamma ya zo kamar wancen lokacin, ya kira ni a waya ya ce yana ƙofar gida, na saka hijjabi na faɗawa Mama ya zo, ta ce"To sai kin dawo". Na fita na same shi a tsaye, fuskar shi babu yabo babu fallasa, babu murmushi irin na wanda yake neman soyayya a wajen mace, na yi masa sallama, ya amsa, a wannan karon na gaishe shi, ya ɗan ɗage gira ya ce"Yau kin ga damar gaisuwar kenan?" Ban ce komai ba. Ya ce"Watanni uku ban gan ki ba, har na cire tsammani tun daga ranar da Baba ya ce ya dakatar da ni, na yi zaton ma kin samu wani ne, sai kuma jiya kwatsam ya kira ni, shin kin amince da auren ne ko kuwa dai kin yarda a yi duk da ba kya sona?" Na kalle shi sosai, babba ne fa ba yaro ba, inda ya yi haihuwa wuri ko bai haifi kamata ba, zai haifi wacce ta kusa kai ni, amma yana abu irin na yara, yaran ma 'yan rainin hankali, kodayake ya same ni ne a araha dole ya dinga gadara. Kamar zan yi shiru, sai kuma na ce"In sha Allahu na gama soyayya, na gama jin son wani har duniya ta naɗe, mutum ɗaya nake so, kuma shi ma soyayyar ta mutu, ba iya soyayyar ba, zuciyata ce ta mutu murus, don haka tambayata ina sonka ma ko kuma ƙoƙarin sakawa na so ka ɓatawa kai lokaci ne, zan aure ka, amma ba zan taɓa sonka ba". Ya ce"Za ki dinga ziyarar shinfiɗata dai ko? Kuma za ki haifa min 'ya'ya, dama wannan kawai nake buƙata daga gare ki, matata tana yi min duka sauran, kuma ita tana sona, sannan albishiinki, ni ma har yanzu ban ji ina son wata mace bayan matata ba, kuma ba na tunanin zan so ki har abada!". Tun da na ji ban ji zafin maganganun shi ba, na tabbatar da gaske zuciyata ta mutu ta fannin duniyar soyayya, tun da Sadam ya nuna ba ni da sauran daraja a idonsa kuma na jure to wane ne zai nuna min ƙiyayya na yi mamaki". Na ce"Ya tabbata auren manufa kake so ka yi da ni, ni kuma zan yi ƙoƙari sosai a zuciyata na kau da hakan, zan saka a raina ni auren biyayya zan yi, domin faranta ran iyayena da suka duba cancantarka suka kawo min kai, ba zan tula musu ƙasa a ido ba, sai dai idan ka zalunce su Allah Ya saka musu". Ya yi 'yar dariya ya ce"Ki kwantar da hankalinki Sayyada, yanzu yaushe ya dace a bar ranar auren? Ni idan son samuna ne a saka sati biyu ma". Na ce"Ka tattauna da iyayena ko yau suka ce a ɗaura a shirye nake". Ya ce"Ok, ki je gida ki kwantar da hankalinki". Na shiga gida, duk yadda na so na manta da kalamansa sai na kasa, ina ta tunanin sabuwar rayuwar da zan shiga, ko me zan tarar? Amma sam hakan bai sa na ji cewar wai zan bijirewa auren nashi ba. Bayan kwana biyu Baba ya ce min sun yi magana daAlhaji Isma'il ya ce yana so a saka rana sati biyu, ya nake gani? Na ce"Baba duk yadda ka yanke ya yi". Baba ya yi shiru yana kallona, kamar dai wanda yake son gano wani abu a tare da ni, kuma na san hakan ba ya rasa nasaba da wannan canjin nawa na lokaci ɗaya. Ya ce"Sayyada me yasa duk kika canza ne? Miƙa wuyan naki da biyayya kamar ya so ya yi yawa, kar fa mu shiga hakkinki". Mama ta ce"Ni tsorona ma ko wani shirin take yi". Na ce"Wallahi ba na shirya komai sai alkhairi, kawai Allah ne Ya shirye ni, kuma in sha Allah daga yanzu zan dinga yi muku biyayya, zan zauna lafiya da duk wanda kuka zaɓa min". Na ƙarasa maganar muryata tana rawa. Baba ya ce"To shikenan, a dai bar shi a wata ɗaya, gobe za su zo da kuɗin aure, zan sanar da su a saka wata ɗaya, ai kamar yau ne, sannan mun yi magana da shi a kan ɗanki, ya ce yana so ki tafi da shi, saboda yana son yara sosai". Na ce"To na gode". Mama ta ce"Tun da an yaye shi ai da an bar shi a nan wajena". Baba ya ce"Tun da shi ya nema a ba shi ɗin". Aka shiga shirin biki, ya ba da kuɗin aure miliyan ɗaya, na ciro kuɗin account ɗina duka na bawa Mama na ce a yi min abin da ya dace, Mama ta ritsa Ni da tambaya a kan inda na samu kuɗin, na faɗa mata wanda Saddam yake ba ni ne tun muna tare, ta ce"Yanzu saura nawa a account ɗinki?" Na ce"Duka ne na ciro babu komai a account ɗin". Ta ce"Ok" A ranta kuma tana ayyana za ta gani idan tsohon kuɗi ko sabo yake ƙara ba ni. Duk sati yake zuwa zance, wanda ba na tsintar komai sai takaici, tun da gadara kawai yake zubawa da kalamai masu kaushi, amma bana nuna masa ɓacin raina, haka har ranar auren ta zo, na ɗinka kaya kala-kala masu kyau da tsada, komai na siya na lefe, akwati ne kawai ban siya ba, kayan ɗaki kuwa ya ce ya yi min, sannan ba ya buƙatar gara, don haka na siya kayan kitchen masu kyau, ƙannaina kuwa su suka dinga kawo min maganin gyara jiki, wanda ni ya dace a ce na kai musu, ina sha ne kawai saboda na kare mutuncina, ba wai don son na birge shi ba, don har yanzu ba na jin wata sha'awa tun aurena da Ustaz ya kashe min ita murus. Waɗanda suka je gidana suka gani suna ta yabawa, ni dai ina ta tunanin sabuwar rayuwar da zan fara, fara ce ko baƙa? Allah masani, na dai saka a raina zan zauna da shi da zuciya ɗaya, na kuma yi masa biyayya daidai gwargwado. 08028066015 [09/11, 8:35 pm] Sadiya Abdulrazak: 40 Da daddare na fito daga wanka a sanyaye, tsirarun 'yan'uwana dake ɗakin suna ta azalzalata saboda sai da motocin ɗaukar tawa suka zo ma na tsiri yin wankan, duk cikinsu Anisa ta fi ba ni haushi, ita ke ta waya da mijinta tun ɗazu, don yana cikin masu ɗaukar amaryar, tana ce masa ga ni nan zuwa a yi haƙuri, a tsanake nake yin komai kamar wata wahainiya, zuciyata babu yabo babu fallasa tamkar yadda fuskata take, ba na cikin farinciki, kuma ba baƙinciki nake yi ba, daidai lokacin da na ɗauki sarƙa ina sakawa a tsanake Anisa cikin fusata ta ce"Haba don Allah Sayyada, kin san mutane nawa ne suke jiranki a nan? Wulaƙanci dai ba shi da daɗi". Na yi mata mugun kallo na ce"Duk wanda ya ga ba zai iya jira ba ya tafi mana, uban wa na gayyata a masu jiran nawa? Ki zaɓi wata cikin ɗakin nan ki lulluɓa mata mayafi ki kai masa mana, kin ga sai ki warware nawa auren ki saka ya sake ni". Ta tsaya tana kallona, ni kuma na cigaba da abin da nake yi, ban damu da maganganun da aka fara yi ba, ana ba ni rashin gaskiya, Anisa ta fice daga ɗakin a sanyaye, na kammala shiri na yafa mayafi, aka raka ni ɗakin Mama, ta ce"Sayyada ai duk wata nasiha da za mu yi miki ni da mahaifinki mun yi, Allah Ya ba ku zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba". Mutanen ɗakin ma suka dinga tofa tasu nasihar, sannan yayar Mama ta riƙe ni har zuwa mota, a karo na uku zan shiga rayuwar aure, kuma ina fatan ya zama na ƙarshe da izinin Allah, hawaye ya kufce min, na share da sauri ina ƙarfafawa kaina gwiwa. Gidan ɓangare ɓiyu ne, part na farko shi ne na uwargida, nan aka fara kai ni, tana falo tare da 'yan'uwanta, duk da ina lulluɓe ban kalli fuskarta ba, amma dai an yi mana karɓa ta mutunci, ana ta addu'ar zaman lafiya da shawarar haƙuri da juna, uwargida ta furta da bakinta ta karɓi amana, za ta zauna da ni da zuciya ɗaya, 'yan'uwana ma suka ba su tabbacin ni ma zan zauna da ita lafiya da biyayya, tun da ba sa'ata ba ce. Aka ɗauke ni zuwa ɓangarena, sai a lokacin na buɗe fuskata na kalli gidana, babban falo ne, wanda ya ƙawati da komai na alfarma, sai ɗakuna guda uku biyu akwai gado, ɗayan kuma a rufe yake sun ce bai bada mukullinsa ba tun da aka zo ganin ɗaki a haka yake, sai yalwataccen kitchen da banɗaki, sannan kowane ɗaki akwai banɗaki a ciki, komai na gidan ya fi na gidan Sadam kyau, tsada, har ma da tsari, amma sam ba wannan ne a gabana ba, saboda ba na son me gidan, kuma ba na jin zan so shi har abada. Kowa ya watse aka bar ni ni ɗaya, wani sabon salo da ban taɓa ji ba, sai ga matar shi ta yi sallama a ɗakina, na amsa ina kallonta, babbar mace a kaina, tun da ni har yanzu a shekara ashirin da shida nake, ita kuwa a kallon da na yi mata za ta yi talatin da biyar, na amsa fuskata babu yabo babu fallasa, na ce"Sannu ina wuni". Ta zauna tana cewa"Lafiya ƙalau amarya, ya zaman kaɗaici da baƙunta?" Na ce"Alhamdulillah". Ta ce"Ma sha Allah, Allah Ya ba mu zaman lafiya, Ya kuma ba ki haihuwa mai albarka". Na ce"Amin, ke ma Allah Ya ba ki". Sai na ga ba ta amsa ba. Muka yi shiru na 'yan mintuna, tana ta danna waya, can ta ce"Ango shiru bai ƙaraso ba, bari dai na kira shi na ji me ya tsayar da shi haka". Ban ce komai ba, ni zaman ma ya gundure ni, ba don kar ta ce na yi mata wulaƙanci ba da tashi zan yi na shiga ɗaki na kwanta. Yana ɗaga wayar na ji mace ta lanƙwashe murya har tana wani rangwaɗa kai gefe ta ce"Hello mai martaba". Na dinga kallonta ta gefen ido, ban ji dai me ya ce mata, sai ta ce"Amarya fa tana ta jiranku, ya kamata ku dawo, kun bar ta da kaɗaici". Shiru na ɗan lokaci, da alama bayani yake yi mata, ta ce"To Allah Ya dawo mana da ku lafiya". Ta sauke wayar ta ce"Ki yi haƙuri, wai wani uzuri ne ya taso masa babu shiri, sai wajen sha ɗaya zai ƙaraso gidan". Na ce"To Allah Ya kawo shi lafiya". Haka muka cigaba da zaman jigum-jigum, ina ta tunanin ɗana wanda Mama ta hana a taho da shi yau ta ce sai an kwana biyu, wannan ce rana ta farko da zan kwana ba tare da shi ba tun da na haife shi, tun ina mazewa har na ji kamar zan fara gyangyaɗi, wajen ƙarfe goma saura kwana na tashi, ganin ita ba ta da niyyar tashi, na ce da ita"Anti ni zan je na kwanta sai Allah Ya tashe mu". Ta yi murmushi ta ce"To sai da safe". Na shiga ɗakin da shi ne nawa, na canza kaya zuwa na bacci na kwanta bayan na murɗawa kofar key, na fara tunanin ranar aurena da Sadam, da yadda ya nuna ba ya zumuɗin kusantata a ranar, duk na damu, amma a yau na ji ba na so wannan sabon mijin nawa ya kusance ni ma, na tuna darena na farko a gidan Ustaz, abubuwan da suka faru a gidan suka dinga dawo min, na fara istigfari, tun ina yi a fili har bakin nawa ya gaza saboda bacci da ya ci ƙarfina. Can cikin bacci na ji ana ta bugun ƙofar ɗakin, na tashi a ɗan razane, na kalli agogo na ga sha ɗaya da rabi, na ƙarasa bakin ƙofar na ce"Wane ne?" Na ji muryar mijina ya ce"Mu ne". Na sauke ajiyar zuciya, na buɗe, da na ji ya ce su ne na yi zaton zan gan shi tare da matarsa ne, sai na gan shi shi kaɗai, gabana ya faɗi ban san dalili ba, raina kuma ya ɓaci, rayuwar aure da wanda ba ka so kuma shi ma ya furta ba ya sonk akwai ƙalubale, na daure na ce"Sannu da zuwa". Na juya zan koma ɗakin, a zatona shigowa zai yi, sai na ji ya ce"Ko zo ki same mu a falo". A raina na ce Ashe dai su biyun ne, to bibiyar me take yi masa? Ni kam zan faɗa mata ta ja shi kawai su tafi na bar mata, na zura hijjabina na bi shi, amma muna ƙarasawa falon sai na ga ba ta nan, na zauna a kujerar nesa da shi, ina kallon gefe, a jikina na ji kallona yake yi, muka yi 'yan sakanni a haka kafin ya ce"Sayyada". Na ce"Na'am". Ya ce"Ba ma son raini, za mu jure komai amma ban da raini, kuma kuma Hajiya Halima ba sa'arki ba ce, idan kika ce za ki raina ta to hatta ruwan gidan nan sai ya yi miki ɗaci, tun tuni mun faɗa miki muna sonta, don haka ba za mu juri ƙananun iskanci ba". Na yi shiru ina ta mamaki, na ce"Amma wannan gargaɗin duk na mene ne? Na ce maka zan yi fitina da wani a cikinku ne?" Ya ce"Ok, mun lura har yanzu akwai rashin kunya a kalamanki, to ki kwantar da hankalinki, nan ba da jimawa ba za ki saitu, amma yanzu ki tafi ki je ki ba ta haƙuri, ki ce ba za ki sake yi mata abin da kika yi ba, idan kuwa kika sake to mun san hukuncin da za mu yi miki". Na haɗe gira na ce"Me na yi mata ne?" Ya ce"Ta ce ta zo ɗakin nan don ta taya ki fira, sai faɗa mata maganganu marasa daɗi, ƙarshe ma kika tafi kika barta a falon". Na yi sororo ina kallon shi, ma ma kasa musawa. Ya ce"Haƙiƙa mun sani rashin kunya halinki ne, to ki sani ba za mu lamunta ba, ki tashi mu je ki ba ta haƙuri". Na ce"To". Na tashi na bi bayansa kamar raƙumi da akala, muna shiga falon, ba ta nan, ya nufi ɗakinta, ni kuma na zauna a kujera ina jiran ganin ikon Allah, tsayin mintuna sai ga su sun fito tare, suka zauna suna kallona kamar yadda nake kallonsu, ya ce"Sayyada mun kawo ki ne don ki kalle ta ko kuma kin zo ba ta haƙuri ne?" Na ce"Hajiya don Allah ko zan iya sanin maganar da na faɗa miki mara daɗi? Wai saboda gana na kiyaye ko". Sai kuwa ya daka min tsawa da faɗin"Ke! Ya isa haka, ba ma son raini fa, ki ba ta haƙuri aka ce". Na danne zuciyata na ce"Ki yi haƙuri". Ya kalle ta ya ce"Kin haƙura?" Ta ce"Mai martaba kenan, ba don ma kun dage ba ni ban so kuka faɗa mata ba, babu komai na haƙura ta ci albarkacinku, ƙanwata ce ba zan yi fushi da ita ba". Ya yi murmushi ya ce"Tana godiya, tana sake neman yafiya, a yafe mata, rashin sani ne da rashin kunya irin na yaran zamani". Na tashi ban ce komai ba na fice daga ɗakin, na yi sa'a bai tsayar da ni ba, na koma ɗakina ina ta mamaki, kenan ita kuma nata salon kishin kenan? Yanzu wannan kissa ce hakan ko mugun hali? Ɗaki na koma na don cigaba da baccina, sai dai babu jimawa na ji dawowar shi, dayake ban rufe ƙofar ba, sai ya leƙo ya ce na fito falon, na tashi cikin ƙosawa ina jin ya fara shiga haƙƙina tun da bacci nake ji. Na manta ma ban tsaya saka hijjabin ba, sai da na ga yadda yake bina da kallo sannan na tsargu, amma na maze na zauna ina cewa"Ga ni". Ya ce"Sayyada barka da zuwa sabuwar rayuwar aure, ina yi mana fatan alkhairi da fatan zaman lafiya, duk da dai ba ma son juna, amma ya zama dole mu mutunta juna, kuma mu bawa juna hakkin da shari'a ta tanadar, hakane?" Na ce"Haka ne". Ya ce"Za ki ga kamar mun kai ki ki bawa Hajiya haƙuri ne saboda ƙasƙanci, a'a sam ba haka ba ne, muna son nuna miki ba zai yiwu daga zuwanki ki fara kawowa wacce kika tarar a gidan nan raini ba, tana da sauƙin kai, kuma duk kishinta ba ta hana mu aurenki ba, sannan muna jin tausayinta, saboda ba ta haihuwa, kuma ba za ta haihu ba, don hakaya zama wajibi ke ka ki girmama ta, ku zauna lafiya, wannan shi ne kwanciyar hankalinmu". Na ce"To in sha Allah". Ya ce"Ina ɗan namu, ya yi bacci?" Na ce"Ban taho da shi ba, Mama ta ce sai an kwana biyu". Ya ce"A'a muna buƙatar shi a kusa da mu da wuri, za a kawo shi gobe in sha Allah, ina son haihuwa, ina son yara, da fatan idan Allah Ya kawo ba za ki gaji ba wajen zazzago su". Na ce"Allah Ya kawo masu albarka". Ya ce"Mun lura jikinki ya fara sanyi ba kamar haɗuwarmu ta farko ba, shin mun fara yi miki kwarjini ne ko kuwa kin fara sonmu ne?" Na ce"Na yi niyyar yi wa iyayena biyayya ne". Ya ce"To shikenan za mu gani". Ya nisa ya ce"Akwai kaza da ake shigowa da ita ta amarci, mun sha'afa saboda yadda Hajiya ta matsu mu dawo gidan, ba mu siyo miki ba, sai ki yafe, ko kuma ki shiga kitchen akwai komai, sai ki gasa ki ci". A raina na ce'Tun da ga ni mayya ba' A fili kuma na ce"Na yafe". Ya ce"To ki je ki yi baccinki, saboda yau mun gaji, ba za mu yi amfani da ke ba, sai dai ko zuwa gobe, ko kuma da asuba ki tashe mu idan kina buƙata". Daɗi ya kama ni, a raina na ce'Allah Ya dawwamar da kai a cikin gajiyar nan' saboda gabaɗaya ba na so a ce wani namiji zai sake kusantata, hakan zai tuna min da abubuwa masu yawa cikin cutarwar da Ustaz ya yi min, na tsani wannan abun da ya kasance samun nutsuwa ga wasu. A fili kuma na ce"To, sai da safe". Na tashi ya ce"Idan kin so ki kwana a ɗakinmu, idan kin so kuma ki dinga kwana a naki ɗakin, kawai dai damuwarmu ya zamana duk lokacin da muka so yin amfani da ke za ki ba mu haɗin kai". Ban amsa ba, na dai tsaya na gama sauraron shi, na wuce ɗakina na kwanta, na daɗe ina tunane-tunane kafin bacci ya ɗauke ni, mai nauyi kuwa. Washegari da na yi sallar asuba ban koma bacci ba, zama na yi ina ta azkar tare da saƙa da warwara, da gari ya waye na tashi na shiga kitchen, na fara kiciniya, na gama komai na gyara gidan tsaf, na yi wanka, na ci abinci, na bar masa na shi a dining, na koma ɗakina na zauna, na ji ana sallama, Hajiya ce don na gane muryarta, ina ji na ƙi fitowa, saboda na ɗauki alƙawarin nesa da ita, kar na fita ta ce na harare ta, gara dai shi ɗin ya riga ni fitowa, da na ji muryarsa alamar ya fito falon, sai na kwanta kamar me bacci, ya shigo ɗakin nawa yana kiran sunana, na buɗe ido ina amsawa, ya ce"Kin yi baƙuwa, ga Hajiya ta kawo mana abun karyawa". Na ce"Ni ai na karya, kai ma ga naka can a dining". Ya tsaya yana kallona na 'yan sakanni kafin ya ce"Sayyada, mun lura ba ki san kan dokar gidan nan ba, ko kuma don ba mu faɗa miki ba ne?" A raina na ce'Wata sabuwa'. Ya ce"To ni sarki ne a gidana, wannan gidan fadata ce, don haka dole ne ki girmama ni kamar yadda za matata take yi, dole ne ki dinga yi min magana da girmamawa, wannan raini ki ce min kai ma, sai dai ki ce ku ma, ni ba sa'anki ba ne, ni shugabanki ne, don haka komai za ki faɗa min sai kin canza harshenki da kalamai masu taushi". Sai yanzu na samo amsar tambayar da na rasa wanda zan yi wa, tun da na zo gidan nan na ji yana yiwa kansa jam'u, kamar wani sarki ko me tare da aljanu, ashe sarauta ce, na ce"To Allah Ya ba ni iko". Ya ce"Ki wuce ki je tana jiranki". Na ce"Na riga na ƙoshi". Ya ce"To ki je ki gaishe ta". Na wuce ba tare da na sake musawa ba, ba don raina ya so ba, na je na zauna na kalle ta, har ta fi ni cin ado kamar ita ce amaryar, na ce"Ina kwana, mun tashin lafiya?" Ta yi murmushi ta ce"Lafiya lau Alhamdulillah, ya kwanan baƙinta?" Na ce"Mun gode Allah". Ta ce"Ga abinci nan na yi muku". Na ce"Mun gode, amma kuma na riga na yi sai dai shi idan zai ci". Sai na ga ya kalle ni da sauri, na kau da kai gafe, Hajiya Halima ta ce"A yi haƙuri ranka ya daɗe tuba take, rashin sani ne". Na yi musu kallon rashin fahimta, kafin na kai ga magana ta ce"Ƙanwata ki gyara kalamanki, kin ce shi, wannan kalma babu girmamawa a cikinta". Nan fa ake yinta, ni ko karatu da kallon fina-finai na gidan saurauta ba na jurewa, saboda girmamawar da suke nunawa idan ta yi yawa abun haushi yake ba ni, ni ko Sarkin gaske na aura matuƙar zai tuɓe a gabana gani nake zai sassauta min mulkin nasa, ballantana wannan da na ya ari sarautar ya yafawa kansa, ko na ce ya ɗorawa kansa wahala, na yi mirsisi ban ce komai ba. Ya ce"Zuba min abincin ni zan ci naki". Ta ce"An gama ranka ya daɗe". Ta shiga kitchen ɗina ta ɗakko plate, ni kuwa na tashi na koma ɗaki, ina jiyo dariyarsu da fira sama-sama, ni kuwa na koma bacci ma. Sai da ya yi shirin tafiya aiki ya tashe ni ya ce min"Za mu fita, idan akwai abin da kike buƙata sai ki faɗa mana ko mu aiko da shi, ko idan za mu dawo mu taho da shi". Na ce"Ba na buƙatar komai". Ya ce"To za ki yi mana abinci kamar na mutum biyar haka, wanda za mu aiko a kai mana kai mana wajen aiki, ya kamata a ce ƙarfe ɗaya kin kammala komai kin ajiye, ki dafa duk abin da kika ga dama amma kullum da daddare tuwo nake buƙata". Na ce"To a dawo lafiya". Ya fita yana cewa"Ki yi magana a kawo yaron nan, ko kuma idan muka dawo daga aiki za mu biya mu ɗauke shi". Na ce"Hakan ma zai fi, ka ɗakko shi kawai". Ya juyo ya yi min wani bahagon kallon da ya saka na tuna da na saɓa dokar shi, na ɗan ɓata rai na juya daga kallon shi". Na fito na wanke kwanukanta, na kai mata, ta karɓa fuskarta babu walwala, na juya na koma ɗaki, kafin karfe ɗaya na kammala girki tsaf, har bakin ƙofar ɗakina mai karɓar ya zo, ya faɗa min shi ne, na ba shi ya tafi, ni ma na ci na zauna na fara kiran 'yan'uwa a waya, can da yamma na tashi na ɗora tuwon, a dole na yi miyar wake saboda babu kayan yin wata miyar, na kammala komai na yi wanka na zauna na kunna kallo. USTAZ Haka nan yau ya ji kewar ganin ɗan shi na wajen Sayyada, yana gujewa zuwa ganin na wajen Rauda don kar ya motsa kishin mijinta, to ita Sayyada tun da bazawara ce ai ba wani abu ba ne idan ya je, ya shirya ya tafi cike da fatan ma Allah Ya sa ta ga ya burge ta, ta sakko su sasanta. A hanya ta tsaya ya cikawa Abiy leda da kayan ciye-ciye irin na yara, ya karasa gidan, ya aika yaro ya ce a ce Malam Ashiru ne ya zo, Baba ya ce a ce masa ya shigo. Ya shigo da sallama aka ba shi wajen zama, ya zauna suka gaisa, Baba ya janyo Abiy dake zaune a cinyar Mama yana cewa"Ga babanka nan ku gaisa mana". Ustaz ya fara yi masa zance irin nasu na yara, ya bashi ledar hannunsa. Baba ya ce"Dama ina son yin magana da kai, ban sani ba ko ka san Sayyada ta yi aure?" Wani abu ya caki zuciyar Ustaz, ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, aure kuma? Wallahi ban sani ba, subhanallah". Mama ta galla masa harara a fakaice, takaicinsa ya sa ta tashi ta shige ɗaki, har yanzu tana ganin baƙinshi idan ta tuna azabar da ya ganawa Sayyada. Baba ya ce"Jiya ta yi aure, kuma mijin nata ya roƙi ta tafi da yaron nan naku, domin yana son yara, kuma ana kyautata zaton zai riƙe mata shi da amana". Ustaz ya yi jimm kafin ya ce"Allah mai iko, yanzu Shikanan ni haka yarean za su ƙare a gidajen wasu ba ubansu ba?" Baba ya ce"To idan ba ka amince ba ai babu dole, kana iya ɗaukarsa ko yau ka tafi da shi". Ya ce"Lala-lala, la ba'asa wallahi, a gaskiya ba ni da mata a halin yanzu, idan ma akwai ban san irin riƙon da za ta yi wa yaron nan ba, saboda haka idan na raba shi da mahaifiyarsa na cutar da shi, Allah ba zai bar ni ba, su ɗauke shi ɗin, amma idan na buƙaci ganin shi zan yi maka waya sai a kawo shi gidan nan na zo na gan shi, tun da dai ai ba za a raba hanta da jini ba". Baba ya ce"Babu damuwa in sha Allah!". Ustaz ya yi musu sallama ya tafi yana cewa"Allah Ya ba su zaman lafiya". A ran shi kuwa cewa yake Allah Ya sa mijin rago ne ta kasa zama da shi ta ji kewar shi ta buwaye ta, a ga ta tsiya. Ustaz bai daɗe da tafiya ba mijin Sayyada ya zo, ya ɗauki yaron ya tafi da shi, da yake yana son mutane sai ya saba da shi bai yi masa kuka ba, a hanya ya tsaya ya yi masa siyayya, duk da ya ga an haɗo shi da ta wajen Ustaz, sannan ya siya kazar amarci ya kama hanyar gidan, a ransa yana rayawa yau zai ji kalar test ɗin mara kunyar yarinyar nan. 08028966015 [10/11, 8:09 pm] Sadiya Abdulrazak: 41 Kafin ya ƙaraso gida sai da Mama ta kira ni a waya muka gaisa ta ce"Sayyada ga mijinki nan ya zo ya karɓi ɗanki, don Allah ku zauna lafiya da mutumin nan, me sonka shi yake son naka, kuma don Allah kar ki tauye masa kulawarki saboda yaron nan, Allah Ya ba ku zaman lafiya". Na ce"In sha Allah Mama". Ina nan zaune na ji me gadi ya buɗe masa gate, ya daɗe kafin ya ƙaraso, hakan ya sa na gane ɓangaren Hajiya Halima ya fara sauka, ya shigo da sallama, na amsa ina kallon ɗana, da yake ƙoƙarin zamewa daga hannunsa zai taho wajena, ya sauke shi yana cewa"Au kenan wariya za ka nuna mana ko Dauda?" Na ɗora Abiy a cinyata ina ce masa "Sannu da zuwa". Ya ce"Yawwa" Yana zama a kujera. Na tashi na ɗakko masa ruwa da lemo na ajiye, zan bar wajen ya ce"Dawo ki zuba mana". Na dawo na zuba masa a kofi, sannan na koma kitchen na kwaso tuwon shi na kai dining, na dawo na ce"Ga tuwonka can a dining". Ya ɗago ya yi min wani kallo mai cike da gargaɗi, ni kuwa a raina na ce wallahi ko dukana za ka dinga yi ba zan dinga yi maka magana da jam'u ba, sarautar taka a wajen matarka kaɗai za ta yi tasiri. Na kauda kai, ya ce"Ok ki kwantar da hankalinki a hankali za ki hau kan hanya". Ya tashi ya kamo hannun yaron, ya nufi wannan ɗakin da yake kulle, ya fara kiciniyar buɗewa, na bi shi da kallon rashin fahimta, na tashi na bi bayansu, ya buɗe suka shiga, ni ma na mara musu baya, domin na ga dalilin da ya sa sai yau za a buɗe ɗakin, turus na yi ganin ɗaki cike da kayan yara, ga gado na yara da sif da madubi, ga kuma kayan wasa nan kala-kala har da kayan ciye-ciye, yaron ya hau murna yana taɓa kayan, ya shagala da kallonsa yana murmushi, ya ɗauke shi ya cilla a gadon yana yi masa wasa, sai na daskare da mamaki. A bazata na ga hawaye ya sakko masa still yana murmushi, ya share, ya juyo ya kalle ni ya ce"Sayyada ga Dauda nan mun ɗakko shi, mun yi alƙawarin za mu riƙe shi da amana kamar ɗan da muka haifa, ba mu taɓa haihuwa ba, kuma muna son yara, suna saka mu nishaɗi ko kallonsu muke yi, muna fatan nan da wata shekarar a ce kin samawa Dauda ɗan'uwa ko 'yar'uwa da za su zauna a ɗakin nan, duk da ba wai muna sonki ba ne kamar yadda ba kya sonmu, amma muna roƙonki ki rayu da mu alfarmar ɗanki da muke son rayuwa da shi, za mu yi miki adalci daidai gwargwado, idan kika yi biyayya kika daina raini da rashin kunya za ki ji daɗin zama da mu". Farinciki ya kama ni, jikina ya yi sanyi, na ce"Na gode, Allah Ya saka da alkhairi". "Babu wata godiya, Dauda ɗanmu ne ai, fatanmu dai a kula da mu sosai, kar a ba shi duka kulawar, duk wani abu da yake buƙata wanda yake nauyinki ne ko na mahaifinsa, ki sanar da mu za mu yi iya ƙarfinmu in sha Allah". Na ce"Na gode sosai". Ya juya ya fita daga ɗakin yana cewa"A zo a zuba mana tuwon, a zauna har mu cinye ko kuma ma a bamu a baki". Ban san lokacin da na harari bayansa ba, a raina na ce Allah Ya kiyaye, na bi bayan shi na zuba masa na zauna ina kallon gefe, ya ce"Ki saka hannu ki ci". Na ce"Na ƙoshi". Ya ce"To daga yau dole ne a dinga jiranmu yayin cin abinci, saboda tare ake ci da mu". Na yi shiru, tun da ban gamsu ba, ba zan karɓi wannan sharɗin ba. Sai da ya kusa gamawa sannan Abiy ya fito daga ɗakinsa, ya fara yi masa murmushi yana cewa"Zo mu ci tuwo Dauda". Raina ya fara ɓaci da wannan kiran sunan shi gatsal, na ce"Ba fa Dauda muke ce masa ba, Abiy". Ya ce"Sunan babanki ne? Sai da muka tambaya aka ce sunan kakan shi ne na wajen uba, to mene ne haɗinmu da shi da za mu ɓoye masa suna?" Na ce"Amma dai a ƙalla ai ya ce masa Dawoud ko". Ya ce"Sayyada mun lura za a sha fama da ke kafin wannan raini da gillin su sauka daga kanki, mun faɗa miki mu fa sarakai ne, a ƙarƙashinmu kike, don haka dole ki bi ra'ayinmu da dokokinmu". Na ce"Ni dai ban ji wani hadisi da aka ce a dinga yi wa miji jam'u ba, don haka sai dai ka bari idan na saba, idan kuma bakina bai juye ba sai ka yi haƙuri da ni". Na yunƙura zan tashi, ya riƙo hannuna ya dawo da ni ya zaunar, ya tsura min ido, ni ma tun ina kallon shi har na ji ya yi min kwarjini, na kau da kai ina ɓata rai, ya ce"Ki kiyaye mu Sayyada, sannan idan muna cin abinci ba a barinmu mu kaɗai, idan kuma ba za ki iya ba za mu dinga kiran matarmu wacce ta san darajarmu tana taya mu ci". Na kwace hannuna na ce"Ai ni zan fi son haka, da ka san da matar taka me yasa za ka zaunar da ni?" Na tashi na koma falo, Abiy ya biyo ni sai ya kira shi, ya ɗora shi a cinya yana ta ba shi tuwon, da suka gama ya zo ya ce"Ga shi sai ki yi masa wanka don ya ji daɗin baccin ko". Na karɓe shi, na yi masa wankan, na dawo falon na zauna, shi kuma ya shiga ɗakinsa, ina kallo ina danna waya har Abiy ya yi bacci Saraki bai fito daga ɗaki ba, na je na kwantar da shi a ɗakinsa, na tofe shi da addu'a, na nemi waje na zauna ina ta tunani, a haka dai wannan Sama'i'lan kamar zai yi mutunci, amma kuma ɗan rainin hankali ne na ƙarshe, ni dai zan yi masa biyayya iya wacce zan iya, abin da ya fi ƙarfins kuma sai na bar shi, na ji daɗi sosai da yadda ya nuna yana son ɗana, hakan ya saka ni ganin mutuncin shi, amma ba dai so ba, ina zaune a nan ɗin na ji ringin ɗin wayata daga falo, na tashi na je na cire ta a caji na duba na ga Sama'ila don da haka na yi saving, na ɗauka duk da na san yana ɗakinsa, ya amsa sallamata ya ce"Dauda ya yi bacci ne?" Na ce"E". Ya ce"To me kike jira kenan? Ki zo ɗakinmu za mu ba ki hakkinki". Gabana ya faɗi, ni fa dama ba auren ba, ina fargabar yadda zan sake haɗa shimfiɗa da namiji ne damuwata, na tsani sex gabaɗaya, haka na daure zuciyata ina tuna hakkinsa ne dole na ba shi, idan Ustaz yana cewa ya yafe min ƙila shi wannan ba zai yafe min ba, murmushi ya kufce min da na tuna wa'azin ustaz mai cike da son zuciya, na sake yin wanka, na shafa humra, na saka rigar bacci na ɗora hijjabi a kai na tafi ɗakin nasa, yana zaune a bakin gadon da counter maƙale a hannunsa yana motsa baki, ya tashi yana cewa"Muna fata da alwalarki". Na ce"Akwai". Ya ce"To Alhamdulillah!". Ya yi min nuni da sallah, na ɗauka na shimfiɗa, ya ja mu sallah bisa sunna, muka idar ya dinga addu'a ina amsawa a hankali yadda ba zai ma ji ba, sai da ya gama ya shafa ya kalle ni ya ce"Da alama da gaske ba kya sonmu, tun da ƙiyayyar har ta kai ba za ma ki amsa addu'armu ba". Na yi kamar ban ji shi ba. Ya hau gadon ya kwanta,ya ce"To sai ki kashe mana fitilar ko, ba ma son haske". Tsoro duk ya kama ni, na shiga damuwa, na kashe fitilar, na nufi gadon na kwanta can nesa da shi, muka yi kamar minti biyu a haka, kafin ya ce"Sayyada, ki matso ko ni ne zan matso?" A raina na ce'Ai kuwa sarautarka ta ci uwar ƙarya ta kwana da yunwa a nan, indai ni ce zan matso ba kai ba'. Na yi kamar ban ji ba, ya sake cewa"Ki matso kusa da ni mana ko ba kya ji?" Ai kuwa na yi kamar ba na ji ɗin ba. Ya ce"Idan ba ki karɓi aurenmu ba ki tashi ki bar ɗakin nan, za mu ba ki lokaci har zuwa lokacin da za ki kawo kanki sai mu yi yadda muke so, amma ki sani ba za mu lamunci raini ba". Ban kula shi ba, kuma ban fita ɗin ba, wajen minti biyar da yin haka sai ji na yi mutum ya matso, a raina na ce'Ashe dai ka matsu'. Tamkar 'yar tsana na zame masa, ya dinga juya ni yadda yake so, tun a romance ya ba ni mamaki, domin ya fi Sadam da Ustaz, amma sai dai jikina ne kawai yake sauraron saƙon ban da zuciya da ƙwaƙwalwata, hakan ya sa sam ban ji daɗi ba, sai ma ƙagauta da na yi ya gama ya rabu da ni, bayan komai ya kammala ya ce"Mun gode da yarje mana, sai dai mun yi Allah wadai da rashin ba mu haɗin haka, amma ki kwantar da hankalinki, a hakan ma za mu dinga bi, tun da dai burinmu shi ne ki samu ciki ki haihu ba wai mu samu nutsuwa da ke ba, ga matar samun nutsuwa can muna da ita, ke kuma sai ki samu nutsuwa da rashin kunyarki". Ban ce masa komai ba, na tashi na bar ɗakin, na koma ɗakina na yi wanka na kwanta, zuciya tana ta bijiro min tunanin Sadam, da faɗa min a yadda yanzu yake sona da zumuɗina inda shi na aura da ba haka daren farkon mu zai kasance ba, amma da na tuna ya yi aure sai na watsar da wannan tunaninna dinga istigfari har bacci ya ɗauke ni, sam ban tantance me na ji a kasancewa da mijina ba, dama tun ina gidan Sadam aka raunata sha'awata da wannan dolen da yake yi min, ƙarshe kuma na zo na auri wanda yake neman rayuwata ma, ya ƙarasa kashe min sha'awar duka. Washegari yana tashi Dauda ya fara tambaya, na ce masa yana ɗakin shi yana wasa, ya zauna kenan zai fara karyawa sai ga Hajiya Halima ta shigo da bata abincin, ta ajiye masa a table ɗin, na gaishe ta na bar wajen, sai kuwa ta zauna suna ta fira, sai bayan ta tafi shi kuma ya koma ɗakinsa na ga bai ci nawa abincin ba nata ya ci, na jinjina kai na fara gyaran gidan, ya fito yana cewa"Mu za ku fita, muna sanar miki yau za ki yi baƙi, 'yan'uwanmu za su zo ku gaisa, mun san kuma suna da yawa, saboda haka ki yi abincin sama da mutum goma, idan ba za ki iya ba, akwai mai taya Hajiya aiki ki je ki ce ta zo ta taya ki". Na ce"To in sha Allah, game da tuwon daren naka kuma, babu cefanen miyar". Ya ce"Ki yi list ɗin abin da za a kawo, sai ki tura mana ta massage za a lawoyin sha Allah". Na ce"To a dawo lafiya". Ya amsa da amin. Sai kuma ya nufi ɗakin Abiy ya ɗauke shi ya yi masa wasa, ya bar ɗakin, na dinga tunanin ta yadda zan je wa wannan makirar matar da batun ta ara min mai aikinta, dai ga shi ma baƙin sun zo da wuri, don ƙarfe goma a nan ta yi musu, har na yi musu tayin karyawa suka ce sun karyawa su goma sha biyu ne, manyan mata da 'yan mata, suka faɗa min yara sai ranar Juma'a za su zo, tass suka yi min bayanin wannan wance ce, ga yadda suke da mijina wannan ma haka, kuma aka yi sa'a sun yi min, don haka na saki jiki da su muka dinga fira, sai dai na ji suna ta kushe Hajiya Halima, har ma suka tambaye ni yanayin zaman namu, na ce ƙalau muke zauna, suka dinga ba ni shawarar to na yi hankali da ita, kar na sake na sakar mata fuskar da za ta raina ni, a bakinsu nake jin mahaifarta ta lalace har ma an cire, don haka babu batun haihuwa, amma ta mallake shi tun tuni ta hana shi aure, sai yanzu da Allah ya yi, ni dai jinsu kawai nake ban faɗi wata magana mai zafi ba ko me sanyi wacce za a kai ni gaba, don mutum mai surutu ba abokin sirri ba ne, kuma ba a cika yin gulma da shi ba. Da lokacin ɗora girki ya yi ina shiga kitchen 'yan mata biyu suka biyo ni, ƙannesa ne uwa ɗaya uba ɗaya, suka karɓe aikin suna taya ni, ɗaya mai suna Mansura ta yi wa ɗayar raɗa a kunne, sai suka fara dariya, Zuhra ta ce min "Anti akwai CCTV camera a kitchen ɗin nan kuwa?" Na ce"Gaskiya ko akwai ban sani ba". Mansura ta ce"Wallahi ko akwai dai na faɗa". Ta ce"Wai kika yi da sarautar Yaya? Kin san fa sarki ne shi a gidan nan nashi, ji yake kamar wata shahararriyar masarauta ce, ko ba ki ji idan zai yi magana yana jam'u ba?" A raina na ce Alhamdulillah, tun da an sosa min inda yake yi min ƙaiƙayi, na ce"Ni dama ina so na tambaye ku, wai ku jinin sarauta ne?" Suka fara dariya duka ce"Wallahi babu ɗaya, matar tashi ce da shegen iyayi tun farkon auren take ce masa sarki, ita ta ɗora shi a wannan tsarin ta ce shi sarki ne, girmamawa kamar ta tsugunna masa, yanzu ai ta rage sosai, shi ne fa shi kuma ya hau kai ya zauna, yake ta famkama, ba ki ga har kayan sarauta yake sakawa ba? To da har doki ma zai siya, Mama ce ta hana shi". Mamaki ya kama ni na ce"Allah mai iko, to ita matar tashi jinin sarauta ce kenan?" Suka ce "Wallahi babu ɗaya, ko akwai sarauta to ta nesa ce, kin san yar Nijar ce ya je ya kwaso ta, ai ni na ji daɗi da ya ƙara auren nan, yanzu za mu dinga zuwa gidan nan a daɗin rai". Haka dai suka dinga surutu, muna yin girki, cikin ƙanƙanin lokaci muka gama, aka yi drink aka saka a firji, kafin a yi sallah, kuma na ji daɗin yadda ba su nuna rashin jin daɗin ganin ɗana ba, duk da ban sani ba ko a gaban idona ne suka nuna haka, mun baje muna cin abinci sai ga Hajiya Halima ta aiko mai taya ta aiki da abinci kula biyu, babbar cikinsu ta ce a mayar ba za su ci ba, wasu kuma suka ce a ci tun da ai kuɗin ɗan'uwansu ba na ta ba, suka dinga sa'insa suna zaginta da yi mata gore-gore, ƙarshe dai aka ƙi karɓa aka koma da shi. Haka muka wuni tare da su, sai yamma lis suka tafi, don har tuwon dare na Sarki su suka yi min, ba ni da kuɗi, don sadakina har Baba zai ba ni na ce ya ajiye min, ga shi account ɗina na babu komai, na kwashe duka a hidimar bikin, sai ƙanwata na kira na roƙi ta ara min dubu ashirin, na yi sa'a aka samu, na aiki yarinya ɗaya ta ciro min kuɗin, da za su tafina tarkato musu kayan kwalliyata da kuma kuɗin na ba su, ai kuwa sai shi min albarka suke, duk mun yi musayar lambar waya da su. Zuwa su ya yi min daɗi sosai, na gyara gidan, na yi wanka na yi sallar magriba, dab da kiran sallar isha'i ya dawo gidan, ina kallon fuskar shi na gane babu walwala a tare da shi, na ce"Sannu da zuwa". Bai amsa na sai ɗaukar Abiy da ya yi yana ɗaga shi sama, ya zauna yana ba shi ledar tsarabar da ya yi masa, na tashi don kawo masa ruwa ya ce"Ke koma ki zauna". Na tsaya ni ban tafi ba ni ban zauna ba, don gaskiya idan ya cigaba da nuna min ikon nan wataran zai sha mamaki. Ya ce"Ko ba za ki zauna ba?" Na zauna ina haɗe gira, ya ce"Ba jiya muka yi muku magana a kan Hajiya ba?" Na ce"To wani abun ta ce maka na sake yi?" Ya ce"Ai kin fi kowa sani, mene ne huruminki a sabgar danginmu da har za ta kawo musu abinci ki rantse ba za a karɓa ba?" Mamaki ya kama ni, don wallahi lokacin da ake maganar ko saka baki ban yi ba. Na ce"Ban ce komai a maganar ba, su ne suka yanke wannan hukuncin". Ya ce"Hajiya za ta yi miki ƙarya ne, ko kuwa mu ne muke ƙaryar?" Na ce"Allah shi yana kallona". Ya ce"Sayyada! Sayyada!" Na ce"Na'am". Ya ce"Tashi ki wuce mu je ki ba ta haƙuri, kuma wannan shi ne karo na biyu da kika mata laifi, idan kika yi na uku za mu ba ta dama ta ɗauki mataki da kanta". Na ce"Na rantse da Allah ban yi mata komai ba, ko jiyan ma rashin sanin halinta ne ya sa na yarda ka saka ni a gaba muka je, amma gaskiya ba zai yiwu na dinga bawa wata zindiƙiya mara tsoron Allah haƙuri a kan laifin da ba nawa ba". Ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Sayyada, a lallai za a samu matsala babba da ke, dole sai an saita ki, kin wuce mun tafi ko sai na ba ki mamaki". Na ce"Ni fa babu wani mamakin gidan aure da ban gani ba". Ya ce"Tashi mu je ki ba ta haƙuri". Da na tashi sai na yi ɗakina na yi kwanciyata, ina jira na ji me zai biyo baya, don na ƙudure ko dukana zai yi ba zan ba ta haƙuri ba. 08028966015 [11/11, 7:13 pm] Sadiya Abdulrazak: 42 Jim kaɗan ya biyo ni ɗakin da sallama kamar abun arziƙi, na amsa ina ɓata rai, ya ce"Ke Sayyada ba ma son raini fa, ki tashi ku je ki ba ta haƙuri". Na ce"Ni fa ban yi mata komai ba, 'yan'uwanka ne suka yi mata, kuma ka kira su ka tambaye su". Ya jinjina kai ya ce"To mun ji ba ki yi komai ba, amma duk da hakan muna ba ki umarnin da ki tashi mu je ki ba ta haƙuri, ai mun isa ko?" Na ce"Ka isa, inda kai zan bawa haƙuri na zan ji ƙyashi ba, ko ban yi maka laifi ba, amma ita dai wallahi ba za ta juya ni ba, tun da ba zamanta nake yi ba, ni ka faɗa mata ma tun da dai abun babu mutunci kawai babu ni babu ita, ta daina zuwa ɓangarena ta daina kula baƙina, duk da 'yan'uwanka ne to ta bari sai sun shiga ɗakinta ta ba su abinci, ka ga ban isa na ce a ce mata ba za su ci ba, sannan kai ma ban yarda ta sake kawo maka wani abinci ba, ba na buƙatar haka, idan kuma nata kake da ra'ayin ci don Allah ka dinga zama a ɓangarenta kana ci". Ya ƙanƙance ido da alamun ɓacin rai yana kallona, da ƙarfi ya kira sunana "Sayyada!" Gabana ya ɗan faɗi ganin ya tsare ni da ido, na tura baki na yi juyi na juya masa baya, babu zato na ji ya damƙo ni, har sai da na ƙwalla ƙara don firgici, ya juyo da ni yana riƙe da ni kuna fuskantar juna ido cikin ido, sai na ga ya yi min kwarjini, na ce"To ka yi haƙuri, ka ce mata na ce ta yi haƙuri". Ya sake ni, ya ce"Wucewa za ki yi mu je tun da mu ba 'yan aikenki ba ne ba ko?" Na ce"Ka yi haƙuri, na riga na rantse ba zan ba ta haƙuri ba". Ya ce"To shikenan, ba za mu karya miki rantsuwa ba, amma za mu yi namu hukuncin, to hukuncinki shi ne yau ba za mu ci abincinki ba, za mu saka ta kawo mana nata shi za mu ci". A raina na ce'Na samu na ɗumame'. Ya fice daga ɗakin, na taɓe baki ina jin ashe ma hukuncin ba mai tsauri ba ne, ko da ya ji na ce kar ta sake kawo masa abinci ya yi zaton kishinsa nake yi da har zan ji haushi don ya ƙi cin abincina? Abiy ya shigo ɗakin nawa, na dinga yi masa wasa har ya yi bacci, na kwantar da shi a ɗakin na tashi na yi sallar isha'i, na koma falo, sai wajen ƙarfe tara ya dawo ɓangaren nawa, na yi masa sannu da zuwa ya amsa, ya zauna, sai ya yi gyaran murya, ni kuwa ko kallon shi ban yi ba, ya ce"Amm... Sayyada, idan kin ji mun yi gyaran murya to muna buƙatar ruwa ne ko lemo ko kuma shi haka". Na ce"To gyaran muryar kala uku ne kenan? Yanzu sai a banbamce min, ka yi min kalar na ruwa, ka yi kalar na lemo da kalar na shayin". Ya ce"Duka kala ɗaya ne, idan mun yi mun sanar, ke ce za ki tambaya me muke nufi". Na yi dariya na ce"To yanzu me kake nufi?" Ya ce"Shayi za ki kawo min, sannan uzurin da zan yi miki na wannan rainin na tsayin sati ɗaya ne kawai, daga nan zan fara nuna miki da gaske ni sarki ne a fadata". Na yi shiru, ban tanka ba, na tashi na je na tafasa masa shayin na kawo masa, na sako tuwo na zauna ina ci, ya ce"Ina Dauda ko ya yi bacci?" Na ce"E ya yi bacci". Ya ce"To gobe kina da baƙi, 'yar'uwarki Anisa da mijinta, ɗazu yake faɗa min za su zo gobe su yi dinner a nan". Na ce"Allah Ya kawo su lafiya". Ya ce"Sai dai kuma gobe ba ranar kwanaki ba ce, Hajiya ce da ni, kin ga sai dai ki je ɓangarenta ki zauna don me girki ita ce mai saukar baƙi". Na ce"Ko baƙin ba nata ba ne? Indai wajena za su zo me zai kai su wajenta?" Ya ce"Haka tsarinmu yake". Na ce"Babu damuwa". Na gama na tashi na tafi ɗakina, na yi shirin bacci na kwanta, can wajen ƙarfe goma kawai sai na ga kira, kafin na ɗaga ta katse alamar flashing ne, na duba abun mamaki sai na ga shi ne, kafin na ajiye wayar sai ga wani flashing ɗin, na ajiye wayata, ai kuwa bawan Allah ya ce mu je, ya dinga flashing babu ƙaƙƙautawa, mamaki ya kama ni, na kira shi, sai ya ɗauka, na ce"Na ga ana ta flashing". Ya ce"Amma dai kin san ba za mu rasa kati a wayarmu ba ko?" Na ce"To amma me yasa ba za ka yi kira ba?" Ya ce"Ba wayar ce buƙatarmu ba, ki zo ɗakinmu za a ba ki hakkinki". Ya katse kiran, na yi turus ina jin ba na son wannan zuwan, amma ba ni da hujjar ƙin zuwa, na tashi na tafi, ɗakin babu haske, don haka na yi lalaube na ƙarasa gadon, ya ce"Sayyada, daga yau idan kin ga muna yi miki flashing to kiranki muke yi, don mu yi amfani da ke, ba wai don ki ɗaga mu yi magana ba". Na ce"To". "Wai me yasa ba za ki dinga kwana a ɗakinmu ba ne?" Ya yi maganar yana janyo ni jikinsa Na ce"Ai zaɓi ka ba ni shi ne na zaɓi kwana a nawa ɗakin". Ya ce"Jiya ba mu ji daɗin yadda kika sakar mana jiki ba kamar gawa, don haka yau ke za ki sarrafa mu". Na yi shiru ina mamaki, a raina kuwa ina raya ashe ba ka shirya ba, ya ƙaraci gadarar shi ƙarshe ya sauke sauke sarautar a gefe ya samawa kan shi nutsuwa, da zan bar ɗakin ya riƙe hannuna ya ce"Yanzu sai gata kenan? Yau kwananki zai ƙare". Na ce"Za ka yi kewata ne?" Ya ce"A'a, kawai dai faɗa miki muke yi ko za ki buƙaci a ƙara ba ki hakkinki, kar mu bar ki da kewarmu ta kwana biyun". Na ce"Ni ba zan yi kewarka ba". Ya ce"Ok, nan gaba za ki yi". Na fita daga ɗakin, ina tunanin me nake ji a game da shi? Akwai alamun zan so shi kuwa? Cikin mu'amalar auren dai ba na karantar komai, amma ban sani ba ko zan samu lafiya a gaba. Washegari tun da sassafe sai ga bugun ƙofar ɗakinmu, a tare muka fito da shi, Hajiya Halima ce cikin ado, ta duƙa ta gaishe shi, ya amsa yana cewa"Hajiya lafiya?" Ta ce"Lafiya lau mai martaba, ranku ya daɗe Allah Ya ja kwana da zamaninku, kewarku ce ta hana ni sukuni, tun da gari ya waye girkina ya zagayo shi ne na kasa jurewa na taho tun yanzu na tafi da ku". Ya fara murmushi ya ce"Ina godiya gimbiya Allah shi albarka, bari na yi wanka na fito". Sai ta shagwaɓe kamar ƙaramar yarinya ta ce"Ni dai mu je na yi muku, kwana biyun nan da ba na yi muku har kun fara yin baƙi". Takaici ya ishe ni, yau ga abun amai ba tashin zuciya, ni fa ba kishi nake yi da kalamanta ba, kawai yadda shagwaɓar ba ta yi mata kyau ba ne abun ya ban haushi, shi kuma da alama burgeshi take, don sai murmushin ƙasaita yake yi. Ya ce"Da gaske mun fara yin baƙi? Kin san fa kin iya wanka gimbiyata". Ta kama hannunshi za su tafi, na ce"Idan ya gama kwana biyu a ɗakin naki kafin ya zo wajena ki cire masa fatar jikinsa yadda ba zai yi baƙi ba". Ya ce"Ke Sayyada". Ta ce"Rabu da ita mai martaba, kun san ku hamshaƙan maza ne, dole ne kishi ya susutata". Ta kalle ni ta ce"Hattara dai yarinya, za ki iya yi min rashin kunya na shanye, amma kar ki sake ki gwadawa yi wa mai martaba, domin kuwa kin taɓo wanda ba ni da saiti idan aka taɓa shi". Ya ja ta yana cewa"Ki huce ranki ya daɗe, yarinya ce, a yi mata uzuri, akwai ƙuruciya". Ta ja shi suka tafi, na bi su da kallo, na taɓe baki na koma na cigaba da baccina. Da zai fita aiki ya shigo, ya ce"Mun shirya za mu fita, akwai abin da kike buƙata ne?" Na ce"A dawo lafiya, ba na buƙatar komai". Ya yi murmushi ya ce"Sayyada kenan". Abiy ya yi wajensa, ya ɗauke shi yana cewa"Ɗana barka da safiya". Sai kuma ya ce"Wai me yasa ba kya kaiwa ɗaya babar tashi shi?" Na ce"Aubdama yana da wata uwar bayan ni?" Ya ce"Tun da kin yarda ɗanmu ne, to ɗan matata ne". Na ce"To ai sai ka bari sai ta nuna ɗanta ne tukunna ko?" Ya ce"Hmm, ki kwantar da hankalinki, wannan rashin kunyar gaba ko an ce ki yi mana ba za ki yi ba". Ya miƙo min wayar shi ya ce"Ki saka min account number". Na ce"Me yasa?" Ya ce"Ba tukuicin daren jiya zamu ba ki ba, ballantana ki dinga yi mana yanga, za mu ba ki ne saboda ko za ki yi baƙi idan kina so ki yi musu alheri, akwai su turare da wasu abubuwan da Hajiya takan siya saboda wannan, idan za ta siya za mu ce ta siyo da ke". Na ce"Ba na so, indai sai ita za ta siyo". Ya ɗage kafaɗa ya ce"Kin huta". Kafin ya fita na ga alert ɗin dubu hamsin, na ce"An gode Allah Ya saka da alkhairi". Ya ce"Ko sau ɗaya ba za ki ce mana mai martaba ba? Sunan yana yi mana daɗi". Na ce"Tun da kana da me faɗa maka ka je ta cigaba da faɗa maka". Ya ce"To na gode". Ya ajiye yaron ya fita yana yi masa bey-bey. Wajen ƙarfe goma sai ga 'yan'uwana sun zo, ƙannaina biyu, maman Anisa, yayar Mama da ƙanwarta, ƙawayen Mama su biyu, da kuma ƙannen Baba su biyu da suke kusa, na kuwa ji daɗin zuwansu, a roƙe su suka wuni, muna ta fira, manya suka yi min nasiha sosai, na turawa ƙanwata kuɗin da na ara jiya, bayan la'asar suka tafi, da daddare ko girki ban yi ba, na ci sauran na rana. Bayan sallar isha'i na ji shigowar mota, na san shi ya dawo tun da har ya leƙo mun gaisa, hakan ya tabbatar min da su Anisa ne suka zo, sai ga shi kuwa ya zo ya same ni ya ce"Baƙi sun ƙaraso, sai ki je ku gaisa a yi dinner gabaɗaya a can ko?" Na ce"Ina gaishe su, amma ba sai na je ba". Ya ce"Ban gane ba sai kin je ba, Sayyada kar fa ki bari mijinki ya yi shaidar rashin kunya, Anisa yar'uwarki ce fa". Na ce"Idan har ita ba ta duba 'yan'uwantaka ta zo mun gaisa ba wallahi ni babu abin da zai kai ni na bi ta ɗakin wata". Ya ce"Shi kuma mijinta fa?" Na ce"Mene ne haɗina da shi? Idan ni ya zo yi wa murnar aure ai ɗakina zai zo ba na wata ba". Ya ce"Hmm, shikenan Sayyada mu ba za mu yi miki dole ba ki je don kanki, Allah Ya shirye ki, amma fa ki kwantar da hankalinki da sannu za ki saitu". Ya bar ɗakin, bayan wani lokaci sai ga Anisa ta shigo, muka gaisa babu yabo babu fallasa, ta ce"Sayyada Allah Ya sanya alkhairi ya ba da zaman lafiya". Na ce"Amin Ya Allah". Ya ce"Ga baban Amir can ya ce ki leƙa ku gaisa". Na ce"Na gode ba sai na leƙa ba". Ta fita tana yi min sai da safe, na bi bayanta da harara, ji nake a raina kamar yanzu da ta zo ta ga alamar ba a cikin tashin hankali nake ba ma haushi za ta ji, tun da na saka a raina hassada take yi min. Bayan sun tafi ya shigo ya ƙaraci faɗansa ban ce masa ta tafasa ba, ƙarshe ya tashi ya ce"Sai da safe, matarmu mai ba mu cikakkiyar kulawa tana can tana jiranmu, wacce take neman hakkinta ba sai an kira ta an ba ta ba". Na ce"Allah Ya sa ka kwana kana sauke mata wannan hakki". RAUDA Zuwa yanzu Rauda ta kai ajin ƙarshe a gajiya, ba dama dare ya yi ta matsa kusa da miji sai ya fara ƙorafin ya gaji, ita kuma ta dage ta ce ai haƙƙinta ne, ƙarshe kuwa abu ya zama faɗa, tana taɓa shi zai tashi zaune ya fara yi mata masifa yana faɗin"Wannan wace irin jaraba ce? Kamar ke kaɗai ce mace lafiyayyiya a duniya? Kamar ni kaɗai ni mai aure? Ba zan yi bacci ba ba zan huta ba kullum mace ta sako ni a gaba da jaraba? To gaskiya Rauda na gaji, duk yadda zan yi da ke ma ba yaba min kike ba, ganina kike yi kawai a lusari, idan kin san ke harija ce ba ki faɗa min ba ban yafe ba wallahi, kin shiga hakkina, ana aure ana ƙiba ni sai ramewa nake kamar wanda kike jan jinin jikina?" Takaici ya ishi Rauda, ga zafin ba gamsar da ita yake ba, ga zafin maganganun da yake faɗa mata, da ma na rashin nunawa ɗanta kulawa, a fusace ta ce"To ƙarya na yi ba lusarin ba ne? Wallahi da zaman aure da kai har gara na san ba ni da auren ma, ban ga miji ba ballantana raina ya biya, basur ya cinye ka da sanyi ka ƙi ka nemi magani?" Ya ce"Au! Haka abun yake? Da gaske da aurena gara babu?" Ta ce"E wallahi, ina dalili to? Babu abin da na nema na rasa a gaban iyayena sai wannan abun, don haka ba zan ɓoye maka ba don shi na yi aure, kuma na zo ban samu ba sai ƙwalele da kake yi min, idan hakane kuwa mene ne amfanin auren?" Ya ce"To shikenan Rauda, ki sani ni ma na gaji, da na san haka kike wallahi da duk son da nake yi miki zan haƙura da ke, ni lafiyata ƙalau don a haka na rayu da matata, ke ce dai harija, kuma cigaba da zama da ke akwai hatsari wallahi, ba zan iya ba, nakasa ni za ki yi, don haka na sake ki saki ɗaya, idan kin samu lafiya kuma da rabon mu zauna sai na sake aurenki, idan kuma shikenan a haka za ki dawwama to Ubangiji Allah Ya haɗa ki da daidai ke". Rauda ta yi shiru jikinta ya yi sanyi, duk da tana ganin sakin shi ne maslaha dama, amma ba ta tsammace shi a yanzu ba, aure bai ci Talata ba bare Laraba ya mutu? Ta tashi ta koma ɗakinta, washegari da safe ta haɗa kaya ta tafi gidansu, sai dai ta kasa faɗin dalilin sakin, saboda kunya ma take ji, amma da aka kira shi mijin sai bai ɓoye ba, ya faɗa musu matsalar da suke fuskanta, kunya kamar ta kashe Rauda, aka gyara zaman idda. USTAZ Allah ne kaɗai ya san halin da yake ciki, ya jigata iya jigata, aure yake buƙata, amma yana ta fargabar idan ya yi ɗin me zai biyo baya? Ba ya so ya yi asarar kuɗinsa a banza, ga shi kuma larurar shi tana ta ƙara baza duniya kar nan gaba auren ya gagara shi, da kuma tunanin ya yi asarar kuɗin shi matar ta kasa zama, duk sai ramewa yake yi a tsaye. A haka dai ya samu wata bazara mai ɗa ɗaya suka fara soyayya, sai da magana ta fara ƙwari ya faɗawa mahaifiyarsa zai yi aure, ta yi tsalle ta dire ta ce Wallahi ba zai yi ba, saboda ɓacin suna ne kawai, ta baza cigiya a samo mace harija mai irin larurar shi,sai dai ya jira idan an samu ya aure ta. Ustaz hankalinsa ya tashi ya ce"Subhanallah! Amma Umma har zuwa yaushe za a samu?" Ta ce"Ko ma yaushe ne, wallahi ba za ka sake auren nan na tonon asiri ba, da sannu za a samu irinka, ni dai ban aminci ka sake aure wata ba, ba zai yiwu ba ka dinga asarar kuɗinka a kan auren da ba ya ɗorewa". Ganin dai da gaske take, ya sa Ustaz faɗin"To shikenan Umma, Allah Ya zaɓa abin da zai zama alkhairi". Ya koma gida a jigace yana fatan Allah Ya sa a samu da wuri. Bai san auren Rauda ya mutu ba sai da ta kusa gama idda, da ya jera kwana uku yana zuwa gidan kullum kuma sai ya ganta, nan direban gidan yake tsegunta masa mutuwar auren, saura kaɗan ya taka rawa a wajen, ya raba dare yana Sallah da addu'ar Allah Ya sa ƙarshen wahalarsa kenan. Ai kuwa da ta gama idda da kanta ta yi masa nuni, ta fara kiran shi da nufin a gaisa, shi kuwa Ustaz me nema a duhu ne a ya samu a sarari, nan fa aka kafa sabuwar soyayya, babu wani ɓata lokaci aka fara batun aure, magana ta je gaban Daddy ya ce ya kawo sadaki kawai a ɗaura, don tun da ya ji dalilin mutuwar auren Rauda ya san mijinta na farko ne ya yi mata wannan horon, shi yasa ya ji daɗin wannan komen nasu, an ba da sadaki aka saka rana sati biyu, tun da ɗaura aure za a yi kawai ta tare ba biki za a yi ba, sai ga shi kuma inda Umma ta ba da cigiyar harija aka ce mata an samu wata bazawara, ita ma zaman aure ya gagare ta, ana da tabbacin tasu za ta zo ɗaya. LITTAFIN NAN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, NA JI WASU SUN CE BA SU SAN NA KUƊI BA NE SABODA TSAƁAR BATI🙄TO NA KUƊI NE, GA ACCOUNT NAN 700 NE 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay 08028966015 [12/11, 8:00 pm] Sadiya Abdulrazak: 43 Ustaz ya je gaida Umma, take yi masa albishir da cewa an samo masa mata, ta ɗora da faɗin"Ka ga yanzu tun da ba a riga an yi auren ba sai ka fasa ka ce ka janye, dama na san za ta koma auren naka ne kawai saboda ɗanta, don haka tun da ka mai irin laurarka ita ya fi dacewa ka aura". Ustaz ya ce"Umma da kafin mu sasanta da Rauda ne haƙiƙa zan so haka, amma yanzu a gaskiya akwai damuwa, saboda ita Rauda ba ta son kishiya, kin san a baya ma abin da ya raba mu kenan, saboda zan auri Zulaiha, yanzu kuma tun da har an kusa aure ai kawai a bar ita waccen ɗin Umma". Umma ta ce"Amma kai yanzu da ka auri wacce haƙurin zama da kai kawai take yi ba gara wacce taku ta zo ɗaya ba?" Ustaz ya ce"Hakane amma Umma ai cancanta za a duba a nan, bi ma'ana ita Rauda uwar ɗana ce, zuri'a ta shiga tsakani, sannan ko don halaccin mahaifinta ba zan iya fasa aurenta ba a yanzu". Umma ta ce"Hakane, to amma fa ni ba zan yi cigiyar nan a banza ba, sai dai ka aure su su biyun ka haɗa". Ustaz ya ce"To ai na faɗa miki inda matsalar take, ita Rauda ba za ta amince ba". Umma ta ce"To ai kuwa sai dai ka fasa aurenta, amma wannan mai irin larurarka ya zama wajibi ka aure ta". Ustaz ya ce"Subhanallah! Don Allah Umma ki fahimce ni". Ta daka masa tsawa da faɗin"Kai! Idan kai ne ka haife ni sai ka cigaba da musawa". Ya rusuna kai ƙasa ya ce"A yi haƙuri Umma a yafe min". Ta ce"Ban ce dole ka fasa wancen auren ba, amma dai za ka haɗa su su biyun ka aura, idan an yi wannan da sati ɗaya ko biyu sai ka auri ita waccen ɗin, Rakiya sunanta, kuma tun yanzu za ka saka rana ka je ka ganta ku gaisa". Ustaz ya ce"To shikenan zan je in sha Allah". Ya yi mata sallama ya tafi gida cike da zulumi, ko da wasa bai faɗawa Rauda ba, don kar ta fasa aurensa. Bayan kwana biyu da maganar ya shirya ya je gidan su Rakiya, har ga Allah ba a yadda ya yi zato ya ganta ba, babba ce don za ta yi sa'arsa ko ma ta girme shi, ga ta ba wata kyakkyawa ba, a taƙaice dai ba ta yi masa ba, sai dai ya aure ta kawai saboda ruwan kashe gobara da ba a yi masa zaɓi, suka tattauna, ta faɗa masa aurenta biyar, ɗanta ɗaya, ya ce"To bambancinmu ƙalilan ne, ni aurena huɗu, amma da gaske mazan ba sa gamsar da ke shi ne silar mutuwar auren?" Ta ce"Da gaske mana, ban san irin halittata ba, tun ina buduruwa dama na san ina da ƙarfin sha'awa, don tun da na balaga kullum ba na iya bacci sai na biyawa kaina buƙata, to da na yi aure kuma na ɗanɗana na ji shi ne komai ya ƙarasa jagulewa, ya zama kawai ni kodayaushe cikin son wannan lamari nake, ni fa ban ƙi a dawwama ana yi ba, sallah da cin abinci kawai nake so a tsaya yi, shi ka don ya zama dole ne". Ustaz ya yi wani murmushi don bai yarda ba, a ransa ya ce'Ƙaryar harijanci kike yi, ba ki aure ni ba ne'. A fili kuwa sai ya ce"Idan na fahimce ki kenan kina nufin sam ba kya gajiya? Idan son samunki ne ma Kar miji ya tafi kasuwa?" Ta ce"Wallahi ban taɓa gajiya ba, ban taɓa jin na ƙoshi da abun nan ba, ai neman kuɗi ya zama dole, zan iya yi maka uzuri ka je kasuwa, amma fa kana dawowa gaskiya babu sake fita, idan da hali ma sallah la yafe ladan jam'i ka dinga yi a gida". Ya yi murmushi ya ce"Allahu akhbar! To Ruƙayya idan kika aure ni da yardar Allah duk abin da kike ji da shi kin tara kin samu, in sha Allah kuma za a saka rana sati biyar idan har a shirye kike kuma ba za ki raina ɗaki ɗaya ba, sannan yanzu aurena ya gabato ba zai kai sati uku ba, idan mun tare da sati biyu sai a yi nakin in sha Allah, nawa ne sadaƙin?" Rakiya wani abu ya daki zuciyarta jin wai zai yi aure nan da sati uku, ta ce"Haba bawan Allah, idan ba da gaske kake ba meyasa za ka ɓata min lokaci? Ta ya zan yarda aurena za ka yi, alhalin ka ce za ka yi wani auren ƙasa da sati uku?" Ya ce"La ba'asa, wannan ba komai ba ne ba ai, ita mahaifiyata ta saka cigiya a sama min irinki, to kafin a samu kuma sai muka sasanta da tsohuwar matata shi ne za ta dawo, kwatsam kuma sai aka ce an same ki, to shi ne yanzu zan haɗa ku biyun na aura". Ta fara girgiza kai ta ce"A'a Malam ba ka shirya aurena ba wallahi, ka ga ni ba zan ƙara yin auren jeka na yika ba". Ustaz ya ce"Kamar yaya?" Ta ce"To me na sama ya ci ballantana ya bawa na ƙasa? Babu wata kishiya ma ni gani nake duk jarabarka ka yi min kaɗan, to idan da kishiya ai har gara ma ban yi auren ba, saboda ƙwalele za a dinga yi min ranar kwananta, ni kuma gaskiya ba zan jure ganinka ban nemi haƙƙina ba, don haka aure ba ka shirya ba, ni babu auren mai mata a tsarina". Ustaz a ransa ya ce"Alhamdulillah!" Saboda dama ba ya son abin da zai ɓata ran Rauda ta ce ta fasa auren. Ya ce"To shikenan tun da kin ce haka, la ba'asa Allah Ya kawo miki mara mata, ni kam dole ba ke kaɗai ba ce gaskiya". Ta amsa da "Amin, Allah Ya ba ku zaman lafiya, ni ma ina zaune daidai ni zai zo". Suka yi sallama cikin aminci, Ustaz ya zarce gidan Umma, cike da farinciki ya zayyana mata yadda suka yi da Rakiya, cewa ta yi ba ta yarda ba, sai da ta je har gidan nasu Rakiya ta sake jaddadawa ba za ta iya auren me mata ba, sannan Umma ta yarda, haka aka haƙura ba don ranta ya so ba. Da ranar ta zo aka sake ɗaura auren Ustaz da Rauda a karo na biyu, tsirarun 'yan'uwa suka kai ta ɗakinta, Ustaz yana cike da farinciki, ga matarsa mai yarda da shi ga kuma ɗansa a kusa da shi, ai kuwa ranar an ci uwar sabada, don sosai suka nunawa kewar junansu, musamman ma shi Ustaz, tun da Rauda ta bar gidan Ustaz sai yai ta ji wata nutsuwa a zuciya da gangar jikinta, yanzu ta ga ingarman miji, da ta je ta auri lagwani da sunan namiji ne ashe, a ranta ta yanke duk tsanani ba za ta ƙara yin sake da auren Ustaz ba, kishiyar ta zo su buga sai dai ta bar mata mijinta,domin yanzu ta san muhimmancin shi, suka fara zamansu na lafiya, kuma Alhamdulillah Ustaz ya rage mammaƙon nashi, tun da ya zo ya ce mata likita ya ce babu damuwa zai iya cin nama da kayan shayi amma baya-baya, ya ƙara da faɗin ya ce ita ma da take da lafiya a faɗa mata ta guji cin nama sau uku a sati. SAYYADA Ranar da ya dawo ɗakina, tun da safen kafin ya fita ya tura Abiy ɗakinsa ya haɗa shi da kayan wasa da kayan ciye-ciye, ya ja hannuna ya nufi ɗakinsa da ni, na bi shi babu musu ina gani abun mamaki, ya rufe ɗakin da mukulli, na ce"Bawan Allah lafiya dai ko?" Ya ce"Ina fa lafiya? Muna can muna tunanin ya za ki yi da kewarmu har ta kwana biyu? Shi yasa domin gujewa ɗaukar alhaki muka ce bari mu fara da ba ki hakkinki tun yanzu". Ya yi maganar yana rungume ni, na yi ƙoƙarin janyewa bai ba ni dama ba, na ce"Wallahi ban yi kewarka ba, sai dai kai ne kewar ta dame ka, kuma kai da matarka take sonka take yi maka komai mene ne abun kewata?" Ya ɗan haɗe rai ya ce"Wato dai Sayyada ba za ki kiyayemu ba ko? Sai yaushe za ki daina danganta ni da kai?" Na ce"Sai ranar da na fara ganin mutum dama da ɗaya a tare da kai, yanzu tun da kai kaɗai ne ba zan fasa ba gaskiya". Ya ce"To daga ranar da kika cika sati ɗaya a gidan nan indai kika sake yi mana magana babu girmamawa to ba za mu saurare ki ba, ki ɗauka kamar kin yi magana da bango ne, babu wannan maganar a lissafi". Na yi shiru ban ce komai ba, ya ƙarasa da ni gadon yana cewa"Ki cire girman kai ki dinga bayyana kewarki yarinya, don mu dai muna da matar da za ta faranta mana, ke kuwa ba ki da ikon samun kowa sai mu kaɗai". Na yi ƙoƙarin ƙwacewa ya riƙe ni gam yana cewa"Sai fa na ba ki hakkinki, don ni adalin miji ne a gareki". Na ce"Na ji ba ni da kowa, amma tun da kai kana da wata don Allah ka daina zuwa wajena, ni na yafe maka hakkin nawa". Ya ce"Yau ga kishi a inda ake iƙirarin babu soyayya, Sayyada anya kuwa?" Daga nan bai sake ba ni damar cewa komai ba, ya shiga yin abin da ya kawo shi, yau kam da alama ya damu da wannan kwanciyar da nake yi masa, ya dinga kama hannuna yana yawo da shi a jikinsa, koya min yake wai ga yadda zan dinga yi na ji daɗi, shi saboda tsabar izza nuna min yake ba fa shi zai ji daɗin ba idan na taɓa shi, ni ce zan ji, ni kuwa na ƙi, amma daga baya sai na tsinci kaina da jin tausayin shi, na fara tunanin shin mene ne laifin shi? Laifin tsohon mijina ne ba nashi ba, na ce ba na son shi, kuma da gaske ba na jin zan so shi ɗin, amma ai na yiwa iyayena lƙawarin zan yi masa biyayya, yanzu ina jin biyayyar? Na yi kaina tambayar, wata zuciyar ta ce ina yi daidai gwargwado, matarsa ta riga ta sangarta shi, ba zan iya wannan rayuwar ba kamar a gidan sarauta, kuma idan ma zan yi ɗin sai dai na fito da salona na da ban ba irin nata ba. Da yamma da ya dawo sai ga shi ya shigo tare da Hajiya Halima, na yi masa sannu da zuwa ita ma na gaishe ta, ta amsa da fara'arta, na ƙarasa na miƙa mata hannu don karɓar jakar hannunta, ta ce"Bar shi ki huta zan kai masa ɗakin". Ta yi hanyar ɗakin Na kalle shi babu walwala a fuskata na ce"Ka dakatar da ita zan yi tambaya". Kafin ma ya yi magana ta dakata, ta juyo. Na ce"Shin wannan ɗakin naka turaka ce ta duka gida da ni da ita namu ne mu biyu ko kuwa ita ma da naka ɗakin a ɓangarenta?" Ya ce"Akwai namu ɗakin mana, kuma da naki da nata kowanne turakarmu ce". Na ce"To a ƙa'idata turakar mijina daga ni sai shi, saboda haka ban amince wata ta ga ko gadon da muke raya sunna ba, daga sanda matarka ta shiga kuwa ya tashi daga turaka ya koma general bedroom, kuma ni da shiga har abada, sai dai ka dinga biyo ni ɗakina ko kuma mu kwanta a falo". Hajiya ta juyo da mamaki haɗe da kishi a fuskarta, amma tana ta ƙoƙarin ɓoyewa sai dai a wajen ni mace ba zan kasa ganewa ba ta ce"Au ashe har akwai wani sirri da ya danganci mai martaba wanda ban san shi ba?" Na ce"Ba kodayaushe ba ne wanda ya riga ka kwana yake riga ka tashi, kar ki yi mamakin na san abin da ba ki sani ba a game da shi, mijinki ne ba mahaifi ko malaminki ne, wannan abin da kike yi yana kawo naƙasu a soyayyarku, kuma ni wannan kissar taki idan kina yi ne don ki ga ƙarshena ya kamata ki dakata haka, kome za ki yi ki tsaya a iya sashenki, kar ki sake zuwa sashena ban gayyace ki ba". Mai martaba ya ce"Ya isa haka Sayyada, mu muka gayyace ta, kuma mun yi ne dama da niyyar a ƙarfafa zumunci, duk wacce take da girki za mu haɗu a ɗakinta tun daga iyanzu har zuwa lokacin da za mu kwanta bacci, sai mu raka wacce ba ta girki, a cikin wannan zaman za a samu tattaunawa da kuma shaƙuwa, tun da mun riga mun zama ɗaya, Sayyada ba na son fitina". Na ce"Na ji ta zauna amma wallahi indai ta shiga ɗakinka to sai dai mu koma raya sunna a falo". Hajiya ta fara taku don zuwa ɗakin nashi, ya ce"Hajiya, kawo jakar mu za mu kai da kanmu, tun da husuma ba ta da daɗi". Ya karɓa ya shiga ɗakin, Hajiya ta zauna a kujera, ni kuma bisa shawarar zuciyata na bi bayansa, na rufe ƙofar na murza key. Ya juyo ya kalle ni, ya ce"Sayyada me yasa kike da fitina ne?" Na ce"Don Allah ba na son ganin matarka a ɗakina, ka je ka sallame ta". Ya ce"Duk kishin ne?" Na ce"A kan me zan yi kishinka? Kawai saboda na san ba zuwan Allah ta yi ba, ba na so". Ya ce"Gaskiya ba za mu iya korarta ba, don haka dole a bi dokarmu, yunwa nake ji me kika dafa?" Na ce"Ban dafa komai ba, amma ban sani ba ko ni kaɗai zan iya ƙosar da kai ba tare da abinci ba?" Ya ce"Me kike nufi?" "Ina so ka ba ni haƙƙina ne". Na yi maganar a raina kuma haushin kaina nake ji, saboda na yi ne ba don ina buƙatar ba sai don na ƙuntatawa Hajiya Halima. Ya yi murmushi ya ce"Da gaske wai?" Na ce"Ƙwarai kuwa ranku ya daɗe mai martaba". Ai kuwa ina rufe baki ya janyo ni ya rungume, ya ce"Sayyada da gaske ke ce". Na ce"To me zan yi muku ku gane ni ce?" Ya ce"To ai gani na yi lokaci ɗaya kin canza ne". Na ce"Ka yi haƙuri, zan canza halina ne daga yau in sha Allah" Sai kuwa ya ɓarke da zance"Na gode sosai Sayyadata, ni fa dama ina sonki wallahi, kawai wannan rainin naki ne ba na so, shi yasa kika ga ina basar da ke, i love You, Please yau dai zan yi zama kamar rayayyiya ba gawa ba ko?" Na yi murmushi na ce"Ran mai martaba ya daɗe kun manta kun daina saka jam'u a maganarku". Ya ce"Ina sane, rabu da sarautar nan, ai a daidai wannan lokacin ke ce sarauniyar ke dai bisimillah Sayyadata". Ai kuwa na zage na dinga faranta masa, yana yi min godiya kamar ba shi ba, da gayya na yi, na yi ne don na ƙuntatawa kishiya, amma wani abun mamaki, sai ga shi a ranar na gane Ustaz fa sumar da sha'awata ya yi ba kashe ta ya yi ba, domin kuwa ta farfaɗo a yau, muka samu gamsuwa sosai, kiran sallar magriba ne yasa muka katse, sai murmushin yake yi yana cewa"Ana yin sallar isha'i za mu ɗora kin ji?" Na ce"To Mai martaba". A tare muka yi wanka, don haka tare muka fita daga ɗakin, na ɗaura zanina sai towel da na yafa shi daga kaina zuwa lafaɗa, shi ma yana sanye da jallabiya kana ganin shi za ka gane ya yi wanka, na ji daɗin ganin Hajiya Halima ba ta yi zuciya ta tafi ba, Ya ce"A, Gimbiya har yanzu kina nan ashe". Ta haɗiye malolon da ya tokare mata maƙoshi ta ce"Ina nan mai martaba, sannunku da fitowa". Ya ce"Yawwa, bari mu je masallaci mu dawo, idan zaman ya ishe ki za ki iya komawa sashenki kawai ma, tun da ai an gaisa". Ta ce"A'a zan zauna". Ni kuwa a raina na ce ashe ba ki gama ganin takaici ba kenan. Na kama ɗana muka shiga ɗakina, na yi sallah, na fito na shiga kitchen na zubawa Abiy tuwo, ita ma na saka mata, ta ce"Ɗauke shi, ai ya ce tare za mu ci". Na ce"Ok" Na zauna ina bawa yaron nashi. Da aka yi sallar isha'i, na yi, na yi kwalliya, na ɗakko rigar bacci fan ɗarinka tsirara na saka, na dawo falon na zauna, Hajiya kallo ɗaya ta yi min ta duƙufa kallon TV, ana sallamawa a masallaci ya dawo gidan, yana shigowa, muka fara rige-rigen taro shi ni da Abiy, ni ce na riga ƙarasawa, na yi tsalle na ɗare shi, ya ɗaga ni yana dariya da faɗin"Yau ga sabuwar duniya ni Isma'il". Ya ce"To yanzu ke ba za ki ci girma ba na ɗauki ɗan namu kenan?" Na fara shagwaɓa na ce"Shi ne zai haƙura". Na kama hannunsa na zaunar da shi, Hajiya ta ɗan zamo daga kujerar ta duƙa ta ce"Sannunku da dawowa, Barka da dare". Ya ce"Au ashe har yanzu kina nan Hajiya, sannu". Na ce"A kawo muku abincin yanzu ko?" Ya ce"E kawo". Na kawo masa, na ajiye ya sakko ƙasa ya zauna, na fara ba shi a baki yana ci, hankalinsa kacokam ya tattara shi a kaina yana ta ci, Hajiya Halima ta tashi ta ce"Sai da safenku". Ya ce"To Allah Ya tashe mu lafiya". Na ce"A haba Hajiya, ko fitar ba mu yi ba kuma? Ni da aka ce sai an fara jin bacci taron zai watse, har ina jin daɗi mun samu ɗan tayin fira, don Allah ki zauna nan da ƙarfe tara". Ta yi min makirin murmushi ba ta ce komai ba ta bar ɗakin, na bi bayanta da gwalo. Na tashi na rufe ƙofar falon, na zare key ɗin, na kai ɗaki na ɓoye, yana nan zaune yana jira na cigaba da ba shi abincin, na nemi waje na zauna a kujera na haɗe rai kamar ba ni ba, da mamaki ya ce"Sayyadata mene ne kuma ya faru?" Na ce"Sayyadarka? Au wai dama kana sona kenan? To idan za ka ƙarada cin abincinka ka ƙarasa, ko kuma ka je matarka ta cigaba da ba ka". Ya ce"Innalillahi, Sayyada me kike nufi?" Na ce"Abin da matarka take nufi shi nake nufi, ai na san wannan duk shirinta, ita ce ta ba ka shawarar a zo ɗakina a zauna, saboda tana son sanin yanayin zaman namu, ko kuma dai tana so ta hana mu rawar gaban hantsi, na san halin namiji ƙila ma ka faɗa mata ba na ba ka kulawa". Ya tsaya yana yi min kallon mamaki, ya ce"Au yanzu dama kina nufin wannan duk kin yi mana ne saboda ki bawa Hajiya haushi? Ni za ki zurma ko?" Ya ture kwanon tuwon ya tashi zai fita daga ɗakin, ya juyo ya ce"Ba ni mukullina". Na ce"Ai kuwa kai da fita sai Allah Ya kaimu gobe". Duk yadda ya kai ga ɓata rai na hana shi, ƙarshe ya haƙura ya tafi ɗakinsa, Abiy ya bi shi, sai da ya yi bacci ya fito da shi ya kai shi ɗakinsa, ina nan zaune a falon, ya ce"Idan kin gama sai ki shigo ba sai mun yi ta flashing ba". Na ce"A gajiye nake, ɗazu ai ka samu garaɓasa ta isa haka". Bai yi magana ba, ya zo ya ɗauke ni cak, ya shige da ni ɗakin, sai da ya sada ni a gadon kafin ya ce"Sayyada maganganun da muka yi ɗazu mun janye su, kamar yadda kika yi komai saboda idon Gimbiyata, mu ma mun yi ne don ta gane muna zaman lafiya kuma muna yi miki adalci, ke ce ba kya yi mana adalci, sannan a matsayin na mijinki idan kika ce har sarrafa ni a gadona ma ba don Allah za ki dinga yi ba zan yi Allah wadai". Daga haka ya ɗora daga inda ya tsaya, sai na yiwa kaina faɗa na shiga taya shi kamar ɗazun. 08028966015 [13/11, 7:41 pm] Sadiya Abdulrazak: 44 Muka samawa juna nursuwa sosai har mamakin kaina nake yi yadda na ji daɗin abun, kamar lokacin da nake gidan Sadam kafin mu fara samun matsala da shi, bayan komai ya kammala sai ya kama hannuna ya ce"Sayyada". Na amsa. Ya ce"Kin ga dai nan a duhu muke, ba kya ganin idona ballantana ki ji kunyata". Na ce"Idonku dai ko?" Ya ce"Zancen serious zan yi miki shiyasa ba zan yi miki jam'u ba, tun da na ga ba kya so". Na ce"To ina ji". Ya ce"Tsakani da Allah kina sona?" Na yi shiru na ɗan lokaci kafin na ce"A'a". "To me yasa?" Ya yi maganar da raunin murya. Na ce"Saboda na kulle zuciyata daga soyayya, ba zan sake son wani ba tun da soyayyar ba ta yi min rana ba". Ya ce"Sayyada wannan ba hujjar da za ki ƙi sona ba ce, kuma ko ba kya sona bai kamata ki raina ni ba, kina jin tsana ta?" Na ce"Wallahi ko kaɗan ban tsane ka ba". Ya ce"To ki karɓe ni a matsayin miji, kuma ki buɗe zuciyarki, sannan ki dinga roƙon Allah ya yi miki zaɓin alkhairi game da rayuwar aurenmu, ki bar mini sauran ki ga ikon Allah". Na yi shiru. Ya ce"Sayyada ina sonki wallahi, wannan halin da kika shiga na Kullewar zuciya a baya ni ma na shiga, amma haɗuwata da matata a hankali sai ta saka na manta da komai, ba zan ɓoye miki ba, ba sosai nake sonta ba, na aure ta ne saboda irin son da ta dinga nuna min, sannan tsananin biyayyarta da haƙuri sun ja hankalina, sai yanzu nake jin irin soyayyar da na san namiji yana ji a kan mace, ita ta nemi soyayyata, ke kuma ni nake neman soyayyarki, ki ja ni a hankali don Allah, za ki iya yi min wannan alfarmar ki zauna da ni da kyautatawa da biyayya ko da ba kya sona?" Na ce"Ba ga shi muna zaune ba". Ya ce"To ai ba kya girmama ni, sai yaushe za ki fara ce min mai martaba?" Na ce"Har abada, ko zan canza maka suna ba dai irin wanda take faɗa maka ba". Ya ce"To wanne za ki faɗa min?" Na ce"Ni fa ba zan soka ba, na gama so". Ya ce"Na ji na yarda, amma ki yi min alfarmar zama da ni, kuma idan Allah Ya kawo mana rabo ki haifa min 'ya'ya, na yi miki alƙawarin indai kika haifa min yara uku kuma kika ji har lokacin ba ki fara sona ba ni zan haƙura na sallame ki ki je ki auri wanda kike so". Na ce"Wallahi ba na son kowa a halin yanzu". Ya ce"To me yasa ba za ki ba ni damar shiga zuciyarki ba?" Na ce"Ka nemo mukullin idan za ka iya ka buɗe ka shiga ka yi yadda kake so". Ya ce"To na gode sosai Sayyada, amma fa sai kin ba ni gudunmawa hakan zai yiwu". Na ce"Zan yi abin da zan iya, amma ban da jam'u tun da kai ba aljanu ba ne". Ya ce"Amma a ce sarki..." Na ce"A wajenta ne kake sarki, ni dai kai mijina ne, kuma idan ka yi haƙuri da sannu za ka ga nawa salon girmamawa da soyayya". Ya ce"Da gaske za ki so ni ɗin kenan?" Na ce"Idan ka samo mukullin zuciyar ba". Ya ce"Muddin kika ba ni dama ta hanyar ajiye wannan girman kan naki cikin lokaci ƙanƙani zan samo shi in sha Allah". Na ce"To Allah Ya sa ka dace". Ya ce"Hmm Allah Ya kawo ranar da za ki furta kina sona ba kuma don Hajiya Halima ta ji haushi ba, ni ai na gano lagonki, gobe ma tare za mu shigo da ita, na yi ta morewa saboda ki ba ta haushi" Na yi 'yar dariya. Washegari kuwa da gaske yake so yake ya samu irin kulawar jiya, don haka ya samu Hajiya da ya dawo ya ce ta zo su je sashen Sayyada, Hajiya ta ce kanta ciwo yake yi ba sai ta je ba, kuma tun daga ranar ba ta sake biyo shi ba, tun daga ranar kuma ta ɗan kama kanta da shiga sabgar Sayyada tun da ta fahimci suna son junansu, ita dai yanzu sallar dare ba ta wuce ta, kuka take tana roƙon Allah kar Sayyada ta haihu da mijinta. Tun daga ranar muka fara zaman lafiya da Mai martaba, ya daina nuna min sai na yi masa jam'u, amma har yanzu shi da jam'u yake danganta kanshi idan zai yi min magana, sai na mayar da abun barkwanci, idan na so tsokanar shi sai na ce"Mai martaba sannunku da dawowa, a kawo muku ruwa?" Sai na kwashe da dariya. Shi ma dariyar yake yi, sai ya ce"Sayyada kenan, da sannu za ki tsinci kanki a komata , ta yadda za ki fara zuba min kirarin sarakai ba tare da kin shirya ba". Ni kuwa na ce"Allah Ya nuna mana, a ranar da na yi maka jam'u na ce maka mai martaba ba da tsokana ko nunawa matarka iyakarta ba, to ka saka a ranka na yi nutso cikin kogin sonka ne, ba sai ka jira na furta ina sonka ba ma". Yanzu sosai muke zama mu yi ta fira da shi, ga shi kullum cikin kyautatawa ɗana yake yi, sai dai ya ce ba zai daina ce masa Dauda ba sai ranar da na saka masa suna, don duk zamanmu duk shaƙuwarmu har yanzu ba na faɗa masa wani suna, sai dai idan zan yi masa magana na yi kai tsaye, a raina kuma cewa nake miji na gari, idan 'yan shaƙiyanci ne sai na ce Sama'ila musamman idan ya kira ɗana da Dauda. Watana biyu a gidan Allah Ya azurta ni da samun ciki, zo ka ga murna a wajen Mai martaba kamar zai haɗiye ni, na ga wata ya zo ya wuce ban yi period ba, sai na sayi tsinke na yi gwaji na ga positive, ban faɗa masa duk da haka, sai da na je asibiti da sunan zan je dubiya, aka yi min gwajin jini aka sake tabbatarwa, na dawo gida da babban albishir, da ya dawo ina dariya na ce"Mai martaba albishirinku". Ya ce"Wata tsokanar kika ƙunso kenan ko?" Na ce"Wallahi sai la amsa da goro". Ya ce"To goro fari ƙal". Na ce"To ka fara ba ni goron albishir ɗin, wayarka nake so kuma". Ya ce"Kin san kuɗin wayar nan kuwa?" Na ce"Ni dai ita nake so, idan ba haka ba na koma da albishir ɗina". Ya ce"Ki fara yi min jam'u zan iya siya miki irin wayata". Na ce"Yanzu nake so, don wannan albishir ɗin ya fi jam'u a wajenka". Sai kuwa ya sha jinin jikinsa, ya fara kallona da zaƙuwa ya ce"Sayyada, mene ne? Wane albishir ne?" Na ajiye masa takardar a cinyarsa, ya kalle ni ya ce"Ta mene ne?" Sai kuma ya duba ya gani, ai kuwa ya yi kabbara, ya yi hamdala, ya yi sujjadar godiya ga Allah, ya ɗago ya ɗaga hannunsa sama ya dinga kwararowa Allah godiya, sannan ni ma ya fara yi min addu'a yana faɗin Allah Ya sauke ni lafiya Ya ba ni duk abin da nake nema, indai aljanna ce ya ɗaga min na shiga, jam'u kuma ya yafe min ba sai na yi ba, har na fara tunanin anya wannan matar ba ta haukata shi ba kuwa? A ce ka ɗaga hannu kana yi wa Allah godiya har da zancen jam'u? Sai da na ga ya fara hawaye, sannan na ɗaga shi, na zaunar da shi a kujera ina share masa, sai ya rungume ni yana cewa"Na gode Sayyada, don Allah ko bar cikin nan ki haihu lafiya kin ji?" Na ce"Allah za ka godewa, kuma shi za ka roƙa ya bar mana shi na haife shi lafiya". Ya ce"Alhamdulillah, yanzu iya wayar tawa kike so ko da wani abun? Na cire layukan na ba ki ko za ki jira na sayi wata gobe na kwashe abubuwa daga ciki?" Ya fara kiciniyar cire cover wayar, na lura nema yake ya zaune fa, ya karɓi wayar na ajiye, na kwanta a jikinsa, na ce"Ka samu nutsuwa, kar ka sa na fara tunanin ranar da na haihu aka damƙa maka yaro ko yarinya a hannu sumewa za ka". Ya ce"Na ji daɗi ne sosai, Alhamdulillah! Ina son haihuwa sosai Sayyada, da kika yi wata ɗaya ban ga alamar ciki ba na fara fargaba, kawai ina ta ɓoyewa ne, ashe abun yana tafe, Allah Ya sauke ki lafiya". Na amsa da amin, da ya ba ni wayar na ce da wasa nake yi, washegari sai ga shi ya siyo min irinta sak a kwali, a cikin satin ya samo min mai taya ni aiki, ya ce bai yarda na sake yin aikin komai ba, tun da ranar da ya san ina da ciki yake ta kaffa-kaffa da ni, ya ƙi kusantata wai tsoro yake kar wani abu ya samu cikin, kuma ina lura da shi yana buƙatata, na fahimtar da shi babu komai ya ƙi fahimta, sai da na tausaya masa na nuna masa ni ce nake buƙatar ya ba ni hakkina sannan ya saki jiki da ni. Kulawa nake samu ba ga shi ba, ba ga 'yan'uwanshi ba, duk sati sai an canza girki daga gidansu an aiko min, ƙarshe na ce ni zan dinga zuwa, don haka duk ranar Juma'a idan zai fita tare muke fita, ya kai ni gidansu, da daddare sai ya ɗakko ni, to a ranar sai abin da na zaɓa zan ci. Tun cikin yana ƙarami muke siyayyar kayan haihuwa, tun da aka samu cikin nan ban sake ganin murmushin Hajiya Halima ko da kuwa na yaƙe ne, don mun sha ma haɗuwa a tsakar gida na gaishe ta ta yi banza da ni, ƙarara take nuna rashin jin daɗinta a kan cikina, ba wai saboda kishiyata ba ce, na saka ta a sahun matan da ba su da adalci, duk mutumin da zai san ba ka haihuwa kuma ba za ma ka haihu ba saboda an cire maka mahaifa, amma ya cigaba da zama da kai da kyautatawa tabbas mai sonka ne, kuma rashin adalci ne zai sa ka yi adawa da samun haihuwar shi, kuma abun mamaki shi sam ba ta nuna masa, tun da yana yawan faɗa min yadda Hajiya ta ƙagauta na haihu, take nuna tana son cikin, har ma ya taɓa ce min idan na haifi wannan a haihuwa ta biyu tun yana jariri za a ba ta ta shayar da shi ya zama nata, ai kuwa nan take na ce ba zan bayar ba, da ya tambayi ba'asi na ce kawai ba zan iya kyautar ɗa ba ne, ban faɗa masa na san ba za ta so ɗan ba, tun da mata masu kissa irin matar nan idan ka fiya nunawa miji ga halinsu gani yake yi kawai kai ne ba ka son zaman lafiya ba su ba. Haka na yi ta rainon cikina har zuwa lokacin da ya girma, hidimar sarki ta ƙara linkuwa a gare ni, indai muna zaune to ya ta matsa min ƙafafuna kenan, da na motsa sai ya yi min sannu, a wannan rainon cikin ne na daina yaudarar kaina, na yarda da gaske Isma'il ya samo wannan mukullin kuma tuni ya daɗe a zuciyata, wallahi son shi na fara yi da gaske, duk da ban furta masa ba shi ma ya gane, wata irin soyayya muka fara yi mara hayaniya a nutse, kuma na ɗaura ɗamarar faranta masa iya iyawata bayan na haihuwa lafiya. Lallai mace tana da rauni, kuma kyautatawa tana kawo soyayya, yawanci matan da suke yin aure ba sa son miji kuma su dawwama da wannan ƙiyayyar to idan ka bincika har da laifin mazan, yau dai ga mijina wanda nake tunanin babu abin da zai yi na so shi yanzu ya yi kane-kane a zuciyata. A kwana a tashi har lokacin haihuwa ya yi, naƙuda ta kama ni watarana, da safe ne ya tafi wajen aiki, misalin ƙarfe goma, mahaifiyarsa ta faɗa min idan na fara naƙuda ita zan faɗawa ba shi ba, saboda ba ta so ya rikice sosai, ai kuwa na kira ta na sanar mata, ta zo da motar gidansu muka tafi asibiti, duk yadda aka so ɓoye masa sai da ya gane, tun da idan yana wajen aiki kafin ya dawo yana kirana a ƙalla sau biyar, tun da aka ce masa zan iya haihuwa a cikin satin, zai ta tambayata ƙalau nake? Ba na jin ciwon komai? To yau kuma da ya kira sai ya ji ƙanwarsa ta ɗaga, ko ta ce ina bacci ko ta ce ina wanka, har la'asar bai same Ni a waya ba, don haka ya zargi ba ƙalau ba, ya taho gida, yana zuwa kuwa Hajiya ta ce ba ta san ma na fita ba, ya tafi gidansu, a can ya ji muna asibiti, dayake ya san asibitin da nake yin awo sai ya tafi kai tsaye, yana zuwa ina haihuwa, ɗana namiji sankacece, don sai da aka yi min ƙari, Isma'il ya dinga murna kamar ya zuba ruwa a ƙasa ya sha, da za a yi min ɗinki na ce a ɗinke ni tsaf, dama ina son gyara jikina, tun da yanzu na yarda Ustaz bai kashe ni ba, don sosai nake jin daɗin wannan mu'malar. Na kwana a asibiti tare da ƙanwarsa bazawara, washegari aka sallame ni muka koma gida cike da farinciki, Mama ta roƙi na dawo gida a yi min wanka, Isma'il ya cire kunya ya ce a yi haƙuri na zauna a ɗakina za a kula da ni kamar ina gidan, Mama ta turo wata 'yar'uwarmu dattijuwa, ita ce take yi min wanka da jaririn da ya ci sunan mahaifin shi Sa'eed, ya ce Baffa za a dinga ce masa, kamar yadda suke faɗawa mahaifin nasu. Ranar da muka dawo Hajiya ta shigo barka fuska cike da yaƙe, ni ce nake gane yaƙe take yi, amma sauran mutane murmushi suke gani, ta zauna a falona ana ta barka da ita, kuma haka kullum take zuwa ta ɗauki ɗan a yi ta fira da ita, sai da ta fara karɓar gashin cibiyarsa ne na ce da me yi mana wankan kar ta sake ba ta ba na so, amma hakan bai saka ta yi zuciya ba. Idan muna zaune da Isma'il ya yi ta faɗa min yadda yake jin tausayinta kenan, ni kuwa hakan bai sa na ji wai zan iya haihuwa na bar mata ɗan ba. Daga kowanne ɓangaren Daddy ya ga gata, kayan barka daga gidansu akwati biyu da nawa da nashi, haka daga gidanmu ma aka ka yi kaya daidai ƙarfinmu, ban da wanda Islma'il ɗin ya ƙaro masa, babu abin da yaron nan ya nema ya rasa. Ana jibi suna sai na wayi gari da alert ɗin kuɗi dubu ɗari uku, wannan karon ba ta POS ma ya tura min ba, da sunan shi ɓaro-ɓaro, tare da gajeren saƙon cewa"Sayyada ina ya garin? Ina yi miki barka Allah Ya raya shi bisa sunna, ga kuɗin gidanki nan". Na sauke numfashi ina ayyana idan an gama taron suna zan mayar masa da kuɗinsa, domin na daina son duk wani abu da ya dangance shi, ba zai yaudare ni da kuɗin haya ba, ya guje ni a lokacin da nake buƙatar shi, yanzu kuwa Allah Ya azurta ni da mijin da zai iya ba ni wannan kuɗin, to me zan yi da na shi? Dama gidan ban yarda ya ba ni shi ba, idan ma da gaske yake na fasa karɓa ya riƙe abun shi. Sai dai kash! Ƙaddara ta riga fata, ana gobe suna an yi min ƙunshi ina zaune sai ga Isma'il ya shigo, hakan ya sa mutanen falon suka watse, zaman shi ke da wuya kiran Sadam ya faɗo wayata, ya ɗauka ya miƙo min, da yake babu saving a lambar, kuma ma ba asalin lambar shi ba ne, tun da na saka shi a blacklist, sai na ce masa ya ɗaga ya saka min a hands free, ya bi umarnina, sallama ta bayyana cikin wayar da muryar Saddam, gabana ya faɗi, yayinda shi kuma ya cewa"Hello Sayyadata, ko har yanzu ba ki huce ba? Ai kya amsawa min tun da barka zan yi miki ko?" Zuciyata ta dinga bugawa da sauri, na kalli Isma'il na ga yadda ya zuba min ido ko ƙwaƙƙwan motsi ya kasa yi, sai fitar numfashinsa da ya canza, ya jefo min wayar a cinyata ya tashi ya bar falon a fusace, na fashe da kuka, kuma har lokacin Saddam bai kashe wayar ba, don haka na fara surma masa Allah Ya isa ina faɗin ba zan yafe masa ba, kuma muddin mijina ya zarge ni har aurena ya lalace sai na yi shari'a da shi, sai ya fara dariya ko a jikinsa yake cewa"Sayyada, yanzu da gaske sai ki yi shari'a da ni? Kenan kin fara son shi ko?" Da sauri na cire ƙunshin hannuna na watsar na kashe wayar, na yi saurin share hawayena ganin mai yi mana wanka ta dawo ɗakin. 08028966015 [15/11, 8:44 am] Sadiya Abdulrazak: 45 Fargaba da kunya suka kama ni, na shiga rashin nutsuwa sosai ga zulumin yadda Isma'il zai ɗauki abun, ko da na haihu bai daina rabon kwana ba, yau ranar kwanana ce, amma haka ya ƙi zuwa ɗakina, ya kwana a wajen Hajiya, bacci rabi da rabi na yi, tsoro fal raina. Washegari suna a masallacin unguwarsu aka yi raɗin sunan, na yi zaton Isma'il zai shigo da safe mu tattauna ko kuma ya ga lafiyar ɗansa, duk da yana fushi da ni, amma sai aiko min da kayan raɗin suna ya yi, wajen ƙarfe goma na kira shi a waya ya ƙi ɗauka, na dinga jera masa kira bai ɗauka ba, na tura masa sako na ce masa ya yi haƙuri don Allah ya zo mu tattauna, shiru bai dawo da amsa ba, na kasa daurewa na dinga hawaye. Shadda kala uku ya ɗinka mana wacce za mu yi ankon suna, hatta style ɗin hotuna da vedios mun gama tsarawa, amma haka Sadam ya rusa min komai, domin kuwa tun fitar da ya yi da safe bai dawo gidan ba sai dare, kuma don wulaƙanci wai sai ga Hajiya Halima tana faɗa wa yan'uwana ya ce duk abin da ake buƙata a tambaye ta, haka aka yi taron suna aka watse ina ta yaƙe. Bai daina rabon kwana ba duk da na haihu, kuma ranar sunan ni ce da kwana, amma haka ya ƙi zuwa sashena, ya kwana a ɗakin Halima, na yi ta kuka ni kaɗai, na sake yarda Sadam ba alkhairi ba ne a rayuwata, guba ne, wanda burinsa ya yi ta azabtar da ni kawai, na ƙara tsanar shi, tsana mai tsanani kuwa, sai yanzu ma nake godewa iyayena da suka hana ni auren shi, kuma suka kwaɗaitar da ni auren Isma'il, sai yanzu nake son mijina da jin ko me zai faru ba zan bari na bar gidan shi ba. Washegari ma ban gaji ba na dinga kiran shi bai ɗauka ba, ko rabon naman suna da aka yi sai Hajiya Halima aka kaiwa nashi, ita kuwa abun nema ya samu sai fiffika take yi tana shan ƙamshi, ni fatana ma a ce bai faɗa mata komai ba, saboda wannan sirrina ne, ko iyaye ban yi niyyar faɗawa ba sai dai idan shi ya faɗa babu yadda zan yi, saboda sun san ni a kan son Sadam, kuma ba sa ganin zuciyata ballantana su yarda na daina son shi. Yau kam na yi niyyar dole sai mun haɗu, don haka dab da zai dawo daga sallar isha'i na fita tsakar gidan na ja kujera filastik na zauna, ai kuwa ana idar da sallah da kaɗan sai ga shi ya shigo, na tashi na tare shi ya ɗan dakata yana kallona, na ce"Don Allah ka tsaya mu yi magana, na gaji da wannan horon da kake yi min". Ya ce"Ba ki da abin da za ki faɗa min Sayyada, tun da kunnena ya jiye min komai ai". Na ce"Wallahi ba haka ba ne, tun da aka yi auren nan bai taɓa kirana ba sai ranar, bibiyata yake yi da sharri". Ya ɗaga min hannu alamar dakatarwa ya ce"Ko kuma kuke biyar juna ba! Na yi bincike tun washegarin ranar na ji wane ne Sadam, na ji irin alaƙarki da shi, da kuma yadda kike son shi, saboda haka ƙarya ne ki faɗa min wai ba ku saba waya a gidana ba, Sayyada ba ki da adalci, shin mene ne laifina da ba za ki so ni ba?" Na katse shi da faɗin"Wallahi ina sonka, wallahi ba ni da sauran alaƙa da shi tun kafin na yi auren nan". Ya ce"Ki je ki yi duk yadda kika tsara, rayuwarki ce, na yi kuskuren tunanin zan iya yin abin da za ki so ni, amma yanzu na gane duk wanda ba ya sonka to ba zai taɓa sonka ba". Ya gota ni zai wuce na tare shi na faɗa jikinsa kuka mai ƙarfi ya ƙwace min, wanda yake fitowa tun daga zuciyata, ya yakice ni ya matsar gefe ya shige sashen matarsa, na koma nawa sashen na tisa kuka a gaba na yi mai isata, tun daga ranar zaman gidan ya ishe ni, na rasa me yake yi min daɗi, kullum sai na kira shi ba ya ɗauka, haka zan yi masa text massage ya ƙi kula ni, ta whatsApp ma babu amsa, kwana biyar bayan suna na yi masa massage na ce ma zan tafi gida, sai ga shi ya dawo min da amsa ya ce Allah Ya tsare hanya, sai ga direban shi ya turo yana jirana, na shiga sabon ɓacin rai, tun da aka yi hakan dole na tafi, don ni da ban yi zaton zai bar ni na, haka na kira Mama na ce mata zan dawo gida na ƙarasa wanka, ta ce sai na zo, muka tafi ko sallama bai bari mun yi ba. Da muka je gida Mama ta gane ba ni da nutsuwa, ta shiga tambayata mene ne yake damuna na ƙi faɗa mata na ce kawai ba na jin daɗi ne, ta tambaye ni dole na yi wa mijina ya bar niena taho? Tun da da farko ya nuna ba ya so, na ce a'a ba dole na yi masa ba, a ranar kuwa zazzaɓin na gaske ya rufe ni, washegari Mama ta raka ni asibiti, muna fitowa daga cikin asibitin sai ga Saddam ya zo shiga, ban taɓa zaton zai iya yi min magana a gaban Mama ba, sai ga shi ya taho inda muke da saurinsa, ya fara faɗin"Sayyada, Sayyadata ashe da gaske kin haihu ko? Yanzu Shikanan kin ci amanata ba za ki dawo mu cigaba da rayuwar aurenmu ba? Kin ga ita ma Safna ta ƙi dawowa, yanzu wa zai riƙe mata 'yarta?" Gabana ya dinga faɗuwa, Mama ta kalle ni ta kalle shi, ya ce"Mama ina kwana, don Allah ki saka baki Sayyada ta dawo ɗakinta, na tura mata kuɗin hayar gidanta ma, amma ta ƙi dawowa". Mama ta damƙi hannuna ta ja ni muka bar wajen, sai kuwa ya biyo mu da sauri yana kirana, Mama tana juyowa ta wanke shi da mari, muka tsayar da adaidaitasahu muka shiga muka tafi, idan ba idona ne ya faɗa min ƙarya ba sai na ga Sadam kamar ba ya cikin hayyacinsa, kuma kamar wanda yake cikin maye, na yi tsuru-tsuru, Mama ba ta yi magana ba har muka ƙarasa gida, Baba yana nan bai fita ba, na yi ɗakina ita kuma ta shiga ɗakinsa, babu jimawa sai ga su sun shigo ɗakin nawa, sai da gabana ya faɗi, saboda Baba bai cika shigowa ɗakina ba sai da dalili mai ƙarfi, na ajiye Daddy da nake shirin shayar da shi na ce"Sannunku". Baba ya ce"Sayyada ashe ba ki rabu da yaron nan ba Saddam? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". Mama ta ce"Ba su rabu ba, domin da alama sun haɗa baki ne za su haɗu a asibiti kamar yadda suka saba, tun da ba ta san zan rakata ba sai da safen nan". Da sauri na ce"Mama na rantse da Allah ba na tare da kowa sai mijina, wallahi na manta da Saddam a rayuwata, ban san ma za mu haɗu wallahi, na canza halina, na tsane shi tun kafin na yi aure". Na fashe da kuka. Mama ta ce"To wane kuɗin haya ne ya ce ya ba ki?" Na fara inda-inda kafin na ce"Ƙarya yake yi, ni babu wani kuɗin haya". Baba ya ce"Kawo wayarki". Na ɗauka na ba shi gabana yana faduwa, sai yanzu na san na yi kuskure da ban goge alert ɗin da massage din ba, wani tsautsayi babba, salatin da Baba ya fara yi ne ya sa na fahimci lallai ya gani, Mama ta ce"Akwai maganar ko?" Ya ce"To ai ba wannan ba, shi ma mijin nata ya sani, ga shi nan tana yi masa massage ɗin ba da haƙuri ya ƙi sauraronta, Saddam ɗin gidanki ya zo ko mijin ne ya gamu da shi a wani wajen?" Ya ƙarasa da daka min tsawa. Na ce"Wallahi babu ɗaya, na rabu da shi da gaske". Ya ce"To ga shi a nan ya ce ga kuɗin hayar ki, ga kuma alert dubu ɗari uku, shin kin sayi gida ne dama ba mu da labari?" Na zayyana musu komai na yadda ya ce ya bar min gidan, sannan na faɗa musu yadda ya kira ni a waya muna tare da Isma'il ɗin, na ɗora da faɗin"Wallahi ba da son raina ba dama ina niyyar mayar masa da kuɗinsa, wallahi na rabu da shi har abada". Baba ya ce"Ai shikenan, yanzu tun da an yi haka ni dai ba za ki saka na dinga jin kunya ba, domin ina ga wannan Saddam ɗin tare kuka rayu a cikin mahaifa, kuka yi gware kuka fito duniya, shi yasa kika kasa rabuwa da shi, zan roƙi mijinki alfarmar ya sake ki kawai, don ba za ki mayar da ni ƙaramin mutum ba". Ai sai na ji wani sabon tashin hankalin, na fashe da kuka na ce"Baba don Allah ka yi haƙuri, wallahi ina son mijina, ban san yadda zan yi da Sadam ba, ya zamar min annoba, ba ni da ƙarfin yakice shi daga rayuwata ni kaɗai sai kun taya ni". Mama ta ce"Tun da mu ne muka taya ki kika kawo shi cikin rayuwarki ko? Ki je ki yi ta yi, kowa ya yi na gari kansa". Na ci kuka a ranar, na shiga damuwa fiye da wacce na ji a gidan Isma'il, sai na ji dama ban dawo gidan ba, tun da ga shi na shiga halin rana zafi inuwa ƙuna. Sosai nake son ganin mijina da don ya kula ni mu sasanta, don haka da yamma na yi masa massage na faɗa masa ba ni da lafiya, Daddy yana buƙatar madara saboda ba ni ma da ƙarfin shayar da shi, Abiy yana ta kuka sai an kai shi wajen shi, kuma ina sha'awar cin wannan balangun da yake siyowa, na kasa cin abinci shi kaɗai zan iya ci. Shiru bai dawo min da amsa ba, har na cire rai zai zo, sai ga shi ana idar da sallar isha'i ya zo, ya shigo har cikin gida, murna ta kama ni, suka gaisa da Mama ta ce masa ya shiga ina cikin ɗakina, ya shigo yana riƙe da Abiy, ya zauna a sallayar da na shimfiɗa, na ce"Sannu da zuwa, da ka zo katifar ai". Bai kula ni ba, kuma bai dawo ɗin ba, yana ta yi wa Abiy fira. Na dinga kallon shi, ya ƙi ko kallonsa, sai yanzu nake jin son shi yana taso min wallahi, na kalle shi sosai ya ba gane kyakkyawa ne, irin kyaun nan nutsattse wanda ba a ganewa a kallon farko, na dinga tuna tarin alkhairansa a gare ni, na ce"Ina wuni?" Bai kalle ni ba, yana kallon hannun Abiy ya ce"Lafiya lau, ya jikin?" Na ce"Babu sauƙi". Ya ce"To Allah Ya kawo sauƙin". Na ce"Allah Ya kawo sauƙi kai ne za ka tabbatar mini da shi, don Allah ka yi haƙuri mu tattauna". Yana kallon Abiy yake cewa"Dauda babarka ta ce kana ta kuka wai kana son ganina, an yi haka ko sharri ta yi maka?" Na ce"Idan ma sharrin ne ka ga laifina?" Ya ce"Miƙo min ɗana, tun da sai na roƙa". Na miƙa masa shi, ya karɓa, ya miƙa min leda ya ce"Ga saƙonki nan". Na shagwaɓe na ce"Ni fa ba shi nake so". Ya ce"Amma ai shi kika ce min". Na ce"Kai nake son gani, don Allah ka saurare ni". Ya ajiye ɗan, ya ce"To idan babu wani abun ni zan wuce". Na fara hawaye na ce"Don Allah ka yi haƙuri". Zai fita na riƙo shi, na rungume shi ta baya gam, muka tsaya a haka tsayin wasu mintuna, ya ce"Idan kin gama sai ki sake ni na tafi, na yi kuskure da na yi tunanin za ki so ni Sayyada, da na san haka soyayyarku ta kasance da Sadam da ban shiga tsakaninku ba, sai dai ina godewa Allah da Ya kau da hankalinki ba ki caka min wuƙa a cinya ba har kika dawo gida". Jikina ya yi sanyi ƙalau, har na sake shi ban shirya ba, na kasa cewa uffan, har ya fice daga gidan, ina ji yana yiwa Mama sallama na kasa ƙwaƙwaran motsi, da ƙyar na ja ƙafafu na koma na zauna, na fashe da kuka, ina tunanin sai yaushe ne tabon laifin nan nawa zai ɓace a idon jama'a, ko shi da na cakawa wuƙar ya yafe min, amma mutane 'yan ba ni na iya sun kasa yafe min, idan har a baya lokacin da ya aure ni bai san rayuwar da na yi da Sadam ba sai yanzu ya sani to na yi masa uzuri, gaskiya dole ya yi fushi da ni, yanzu na gane ashe babu wanda zai ji abin da na aikata ya aure ni ya riƙe ni da zuciya ɗaya, sai irinsu Ustaz wanda su kuma za su zauna da ni ne saboda biyan buƙatarsu. Kunya ta saka ban sake neman shi ba, ban sake yi masa massage ba, shi ma kuma bai sake zuwa ba har aka yi sati ɗaya, cikin kyautar kuɗin da yake yi mini na turawa ƙanwata Khadija dubu ɗari da hamsin ta siyo min ingantattun magunguna na gyaran jiki da maganin sanyi, ba duƙufa amfani da su kamar an ce min zai zo ya ɗauke ni a cikin satin. Mama ta fara maganar zan koma ɗakina tun da ba wankan ne ban iya ba ai, nan fa hankalina ya tashi, saboda gaskiya ba na son komawa ba tare da mun gama sasantawa ba, don zaman zai yi min ƙunci a ce kishiya tana kallo ba ma jituwa da miji. Don haka na kira shi bai ɗauka ba, na yi masa massage na roƙi ya zo ba ni da lafiya, sai ya dawo min da tambayar "Mene ne maganin rashin lafiyar ki a tare da ni wanda yasa kike son ganina don ba ki da lafiya? Ko kuma kuɗin ganin likita ne babu na turo miki?" Na mayar masa da amsa na ce"Komai na jikinka maganina ne, kuma ai ka sani rashinka ne ya kawo cutar". Bai dawo da amsa ba, amma da daddare sai ga shi ya zo. Yana shigowa na ce"Sannunku da zuwa ranku ya daɗe, ya hanya?" Bai amsa ba ya zauna, na ɗakko ruwa a ɗakin Mama na dawo na ajiye masa na ce"Ga ruwa ku sha". Bai sha ba, bai yi magana ba, sai dai ya ƙarasa yana kallon ɗan shi dake bacci a cikin net, na ce"A ɗakko muku shi?" Ya ce"Rabu da shi kar a tashe shi". Na yi raurau da ido na ce"Mai martabaz tuna nake ranka ya daɗe, kaina bisa wuya, don Allah a gafarce ni ba don halina ba, a sakaya ni a unguwar adalci ku irin na sarakai masu adalci ga matayensu, ku yi haƙuri ki yafe ni, Allah Ya huci zuciyarku ranku ya daɗe". Ya ce"Amm... Sayyada mun shaida yau kin yi mana biyayya, kuma kin miƙa wuya ba tare da shaƙiyanci ba, to sai dai kuma kin makara domin a halin yanzu ba ma buƙatar jam'u daga gare ki, na matarmu ma kaɗai ya isa, zai fi ki zauna a matsayarki na cewar ni ba sarki ba ne". Na fara hawaye da gaske babu wasa, saboda neman duk wata hanya nake yi da za mu sasanta na ce"Tuba nake ranku ya daɗe, a baya shaɗain ya yi tasiri, na yi rashin kunya, ina neman gafara, a gafarce ni ranku ya daɗe sarki mai mulkin gidansa, mai Hajiya Halima uwar kissa, mai matar so Sayyada, an gaishe da uban Dauda da Daddy, da yardar Allah sai ka ga 'ya'yanka dozin da jikoki babu adadi, tuba nake,a dubi rafkananniyar zuciyata ba za ta iya ɗaukar fushin Saraki ba, wane mutum inji mutuwa". Duk yadda ya ɓata rai ya so daurewa sai da murmushi ya kufce masa, amma ya maze kamar bai yi ba, ya tashi yana cewa"Ki shirya gobe ƙarfe goma na safe zan zo mu je wani waje". Zuciyata kawai ta raya min gida zai mayar da ni, don haka na ce"Ina godiya, godiya nake ranku ya daɗe, Allah Ya ƙara girma". Na raka shi har ƙofar gida ina ƙara yi masa kirari kamar maroƙiya, na kwana da zulumin goben idan mun koma magana ta mutu ne ko da saura? Ban yi bacci ba sai da na haɗa mana kayanmu tsaf. Shi kuwa da ya koma gida sai ya tsinci kansa da kewar Sayyada fiye da ta kullum, don haka yau a sashenta ma ya kwana, duk yadda Hajiya ta yi da shi ya ƙi yarda, ya ce ta rabu da shi a can ɗin, bayan ya gama komai ya kwanta ya kunna recording ɗin firar su da ita, yana ta murmushi, musamman da ya tuna yadda take yin abin bil hakki ba da shaƙiyancin da ta saba yi masa ba, wani furucinta ya tuna, wanda take cewa 'A ranar da na yi maka jam'u na ce maka mai martaba ba da tsokana ko nunawa matarka iyakarta ba, to ka saka a ranka na yi nutso cikin kogin sonka ne, ba sai na la jira na furta ina sonka ba'. Murmushinsa ya ƙara faɗaɗa ya furta"Ina son matata Sayyada". Ya nemo wata lamba ya yi kira, suka gaisa, ya ce"D.S.P akwai wani yaro da nake son ya kwana a hannunku yau gobe ina da meeting da shi, zan turo maka address ɗinsa yanzu don Allah". Daga can ɓanagren aka ce"Ka ƙaddara kamar an gama indai yana cikin Nigeria". Ya ce"Godiya nake yallaɓai". Ya tura masa address ɗin, har ya fara bacci ya kira shi ya faɗa masa ya shiga hannu, sannu ya kunna data akwai saƙo, ya kunna data, sai kuwa ya ci karo da vedio, Saddam ne zaune da kwalbar giya yana ta maye da surutai marasa kan gado, a haka suka tarar da shi suka ɗauke shi, Isma'il ya runtse ido, bai taɓa jin tsanar wani a duniya kamar yadda ya tsaki Saddam ba, kishi yake yi da shi mai tsanani, ya turawa Sayyada vedion tare da gajeren rubutu ya ce"Yanzu wannan ne ya saka kika ƙi sona ko?" Sai da asuba na ga saƙon, domin fa wuri na yi bacci, na cika da mamakin inda ya samu vedion, amma ban yi mamakin ganin Saddam cikin maye ba, saboda dama a yadda ya tare mu ni da Mama na zargi ya fara zuƙe-zuƙe. Ƙarfe goma da mintuna ya zo gidan, na faɗawa Mama dama ya ce zai zo mu je wani waje, ta ce"To a dawo lafiya". Ya ce"Sayyada Dauda ya zauna a gida, ba daɗewa za mu yi ba". Na ce"Au wai ba gida za mu koma ba?" Ya ce"Ban sani ba". Na ce"A huce ranki ya daɗe". Na koma na lallaɓa Abiy ya zauna, sai kuma na shiga tunanin ko kewata ya yi yake so mu ɓarje amarci shiyasa? Wani zumuɗi ya kama ni, domin ni ma na yi kewar tashi ba kaɗan ba kuma na riga na samu tsarki. 08028966015 [16/11, 10:21 am] Sadiya Abdulrazak: 46 Shiru a motar bai kula ni ba, na gyara zama na ce"Sultan". Ya ce"Wane kuma Sultan?" Na ce "Sabon sunanka ne, ai na faɗa maka ba zan bi abin da matarka ta ƙirƙira ba, sai dai na samu nawa da ban". Ya ce"Indai ba za ki ce min mai martaba ba to ki bar shi, ni shi nake so". Da yake zaman lafiya nake nema sai na ce"To an gama ranka ya daɗe". Ya wani taɓe baki ya ce"Kirarin ya fi daɗi a bakin matata". Ban ce komai ba, amma a raina na saka wallahi sai ya biya bashin wannan basar da ni ɗin da yake yi, bari dai komai ya wuce na koma, zai gane ni ma da tawa sarautar. Ganin mun ɗauki wata hanyar ba gidanmu ba ya sa na tambaye shi ina za mu je? Ya ce"Kin nuna min wannan tantirin tsohon mijin naki shi yake bibiyarki, to ba zan juri haka ba, shi ne nake so hukuma ta yi maku tsakani, tun da dai ba za mu ɗauki doka a hannunmu ba ko?" Duk da zan so hakan, amma sai da na ji gabana ya faɗi, na ce"Hakane". Ya ce"Idan akwai wani abun da ya kamata na sani ki sanar da ni". Na ce"E, sai dai maganar kuɗin haya". Ya kalle ni da mamaki ya ce"Kamar ya kuɗin haya? Wane ne yake yi wa wani haya?" Na ce"Dama shi ne ya ce ya bar min gidanmu da muka zauna a ciki, shi ne yake turo min kuɗin haya". Ya ce"Ina takardun gidan?" Na ce"Bai ba ni ba, suna wajen shi". Ya ce"Bayan aurenmu ma ya turo miki?" Na ce"E, ana gobe zai kira ni ɗin ya turo min ɗari uku". Ya yi min wata kafirar harara ya ce"Hmm, na gode Sayyada". Na ce"Don Allah ka yi haƙuri, ai dama ina da niyyar mayar masa to ba ni da account number shi ne". Ya ja dogon tsaki "Ya isa haka, ki rufe min marakunyar bakin nan naki, ɗari ukun banza! Hmm wannan ya nuna min har yanzu ba ki gama karɓa ta, kuma lokaci ya yi da zan kama kaina, don na yi iya yi na, dama tun da ba kya sona tun farko na san ba lallai ne ki yi min adalci ba". Jikina ya yi sanyi, na fara hawaye. Ya zaro tisue a gaban motar ya jefa min, kafin ya ce "Ni ba kuka na ce ki yi min ba, ban da rashin adalci Sayyada idan kina buƙatar kuɗin me yasa ba za ki tambaye ni ba? Kuma batun ya ba ki gida ƙarya yake yi, idan niyya ya yi ya bar miki ai zai ba ki takardun a hannunki kuma ki cigaba da karɓar kuɗin hayan, ba dole sai kun cigaba da connecting da shi ba, da haka ya yi zan yarda kyautatawa ce ta sa ya ba ki, kuma ba zan yi fushi ba, tun da ai ba wani abu ba ne don miji ya bawa matarsa gida kyauta a lokacin da suke tare, to amma shi na shi akwai manufa!!!" Ya ƙarasa da ƙarfi har yana buga steering motar. Duk na firgita na ce"Ni dai ka yi haƙuri". Ya ce"Ba zan yi ba, na ƙi haƙurin, kuma wallahi Sayyada sai kin sha wuya kafin ki samo kaina". Murmushi ya ƙwace min, na guntse bakina bai gani ba, saboda tuna yadda daga gwada shi don na ƙuntatawa matarsa ya gigice, ballantana yanzu da nake shirin ɗana masa babban boom ɗin da zai rikita masa lissafi, amma ban sani ba ko dai zai jure da gaske. Muka yi shiru har muka ƙarasa bai sake magana ba. Kuɗi sun yi a rayuwa, har mamaki na yi yadda ake ta girmama shi kamar mai marbatan gaske, aka ba mu wajen zama, ya kalle ni ya ce"Saura a fito da shi ki dinga kallon shi, laifikanki yawa ne da su a wajena, don haka ki bi ni a hankali, ba ni wayarki". Na miƙa masa bayan na buɗe, ya fara danne-dannen shi, na ce"Ni ma ai sai ka ni taka". Ya harare ni bai ba ni ba ɗin, muna nan zaune aka kawo Sadam, to ido ba a yi masa shamaki don haka dole sai da na kalle shi, a kallon kuma na ga yadda duk ya rame, ko riga babu a jikinsa amma babu alamar an dake shi dai, ya zauna yana ɓata rai, na kau da kai daga kallon shi, ɗan sandan ya ce da Isma'il "Alhaji ga shi nan, mene ne a tsakaninku?" Isma'il ya ce"Yallaɓai tambayar shi za ku yi a tsanake mene ne yasa yake bibiyar matata don ya kasance tsohon mijinta? Sun rabu babu ko ɗan tsako a tsakaninsu, yanzu ta yi aure a kan me zai cigaba da bibiyarta har yana tura mata kuɗi kamar wata almajira? Ga shi nan dai ya yi muku bayani da bakinsa". Saddam ya yi shiru yana ta ɓata rai. Ɗan sandan ya talli ƙeyarsa"Ka yi mana bayani, me yasa kake bibiyar matar aure?" Buɗar bakin Saddam sai cewa ya yi"So ne". "Kai kafiri ne da ba ka san hukuncin son matar aure ba? Ko ba ka san laifi ba ne a doka?" Ya tambaye shi a tsawace Babu alamar damuwa a tare da Saddam ya ce"Ai matata ce, kowa ya san Sayyada tawa ce, kawai don mun ɗan samu hargitsi silar na yi aure shi ne har ya je ya aure ta, don haka ya sake ta kawai shi ne mafitarsa". Tass! Aka wanke shi da mari, gabana sai faɗuwa yake yi, Isma'il ya tashi a fusace ya ce"Ku yi duk abin da ya dace, ku daina dukan shi". Zai bar wajen, ɗan sandan ya dakatar da shi yana faɗin"Ka yi haƙuri Alhaji, dama don ka hana a dake shi ne, da ya yi laushi tun jiya yau ba zai samu damar faɗin haka ba". Na kalli yadda yake kallon shi yana huci, shi kuma Saddam ƙasa yake kallo fuskar shi babu alamun nadama ko kaɗan". Ɗan sanda ya ce"Ka ba mu dama mu kwana uku tare da shi a nan, idan ya yi laushi ya dawo nutsuwarsa sai ka dawo a yi sasancin". Isma'il ya ce"A'a a yi masa warning kawai". Sadam ya ce"Kar a ƙyale ni, ka saka su kashe ni, mene ne amfanin rayuwata dama indai zan zauna ba tare da Sayyada ba? Na riga na sha gabanka, taƙamarka da kuɗinka na banza ne, tun da ba su ba ka budurcinta da soyayyarta ba, ko yanzu idan aka buɗe zuciyarta soyayyata kaɗai za a tarar a ciki, tana zaune ne da kai saboda na ƙi ta, ba don tana sonka ba, kuma yanzu ma ai kai rago ne ba jarumi ba, da sai ka ba ni dama mu fafata a shiga takara a ga wanda zai yi nasara da ni da kai, shashashan banza, har ka mutu ba za ka ji daɗin Sayyada kamar yadda na ji ba". Ni dai daga nan na tashi na fice da sauri ina kuka, ganin yadda Isma'il yake wata tsuma jikinsa yana karkarwa. Ɗan sandan ya kai masa wani naushi a baki, nan take bakin ya fashe, Isma'il ya ce"Ku kulle shi, idan ya gaji da zaman sai ku faɗa min a yi maganar, ku ce ya ba da account number shi". Saddam ya ce"Ba zan bayar ba! Ita ta ce maka ba ta da buƙatar kuɗin ne? Tun kafin ka santa nake ba ta tana karɓa, kai ba ka isa ka hana ni ba". Isma'il ya jinjina kai ya fita daga wajen, ransa a matuƙar ɓace. Ina tsaye a jikin motar ina kuka ya zo, ya buɗe ya shiga, ni ma na shiga, yana ta huci, ban taɓa ganin shi a irin wannan ɓacin ran ba, hannunsa yana karkarwa ya fara tuƙa motar, ga shi ban iya mota ba ballantana na karɓa na ja, tsoro duk ya kama ni na ce"Ko za ka bari sai ka dawo cikin nutsuwarka sai mu tafi?" Ya yi min wani mugun kallo mai cike da gargaɗi, na ce"Don Allah ka yi haƙuri". Bai kula ni ba har muka ƙarasa gida, ya ajiye ni, har ƙofar gida, ya ba ni wayata, na zauna na ƙi fita ina kallon shi, na ce"Ka yi haƙuri, na fi ka shiga damuwa". "Ai dole ki ba ni haƙuri tun da wani ɗan iska kina ji ya yi min gorin karɓar budurcinki da kuma nuna ya fi ni saduwa da ke, da matata ce ta yi miki wannan gorin sai kin yi mata rashin kunya". Na ce"To ya zan yi? Ai ba da son raina ba, idan ban ba ka haƙuri ba me zan ce maka?" Ya ja tsaki ya ce"Fice min dalla!". Na fita da sauri, sai dai zuciyata ta karye, kafin na shiga gidan kuka ya ƙwace min, Mama ta taso da sauri"Subhanallah! Sayyada, me ya faru? Ke da wa?" Na ƙara ƙaimin kukan nawa na dinga yi, ta kunce goyon bayana ta saka shi a kafaɗa ta ce"Tambayar ki da nake me ya yi miki?" Cikin kuka na ce"Saddam ne, Mama zai kashe min aure, wallahi idan auren nan ya mutu na haƙura da aure har abada". Na sake rushewa da kuka, na yi ɗaki a guje. Mama ta rabu da ni, sai da na gama kukan sannan ta ritsa ni da tambayar me ya haɗa mu da Saddam ɗin? Na kwashe komai na faɗa mata, sai kuwa ta hau salati kafin ta rufe ni da faɗa tana faɗin ni ma da nawa munafurcin da kwaɗayi da son zuciya, ban da haka a kan me zan yarda ya ba ni gida har da karɓar kuɗin haya kuma duk ban faɗawa kowa ba, cikin kuka na ce"Mama a lokacin ina buƙatar kuɗin, ina gidan baban yaron nan babu abinci mai kyau, ba ni da lafiya ma ya ƙi kai ni asibiti shi ne na taɓa kuɗin". Mama ta fusata"Kin faɗa mana ba ki da lafiya? Ko kin roƙe mu kuɗi ba mu ba ki iya ƙarfinmu ba?" Na ce"A lokacin Baba yana kan ganiyar fushi da ni, idan na cika kawo cikas ɗin shi cewa zai yi fitina ta ɓullo daga gare ni, kuma zai ce ban yi masa biyayya ba ban karɓi auren ba, shi yasa na bar matsalar a cikina". Ta ce"Duk da hakan, ai kin san ni zan fahimce ki, kuma wanda ya ba ki a karo na biyu fa? Wace matsuwar ce ta sa kika karɓa?" Na ce"Wannan na yi laifi, kuma don muna tare ne a lokacin shiyasa na karɓa, tun da ai bai fi kyauta ba". "Shi kuma na ukun nan fa? Da me mijinki ya rage ki? Ko kuma har yanzu kuna tare da shi kuma soyayyar?" Na girgiza kai da sauri"Wallahi bai rage ni da komai ba, kuma bai yi shawara da ni ba kawai kuɗin na gani, ku yafe min, tabbas ni ce na janyo Saddam rayuwata, ga shi baƙincikinsa yana ta bibiyata, ku saka baki kar aurena ya mutu, ya fusata sosai". Mama ta ce"Ke ce kika ja komai, kai sanin wannan Saddam bai yi mana rana ba". Ta tashi ta bar ɗakin, na yi jugum abun duniya ya ishe ni, wajen azhar na kira shi bai ɗauka ba, na tura masa saƙon ban haƙuri da jam'un da yake ƙauna, bayan la'asar ma na kira shi nan ma bai ɗauka ba, duk na shiga damuwa, na dinga bin shi da massages amma shiru. Da Baba ya dawo Mama ta sanar da shi halin da ake ciki, sai ya yi shiru ya ƙi cewa komai saboda takaici, ba tun yau ba na gama yarda da cewar duniya za a daɗe ba a samu maƙiyin Saddam da ya kai Baba zafafawa. Wasa-wasa sai da aka yi kwana biyar cif mai martaba bai zo ba, kuma ba ya ɗaukar wayata, tun ina yi masa saƙon har na gaji na rabu da shi, don ni ma na yi fushi, na fara tunanin ba sona yake yi ba, idan har kishi ne ai ya ci a ce ya sakko ya yafe min, tun da ba ni ce na yi masa gorin ba. A rana ta shida sai ga shi ya zo gidanmu, babu zato babu tsammani, farinciki ya kama ni, amma na yi burus ban nuna ba, saboda ya ba ni haushi, sai ga shi bai ma neme ni ba, da Baba kawai ya yi magana ya yi tafiyarsa, hakan kuwa ya ƙara ɓata min rai, ga shi duk yadda na so na cire shi daga raina ya daina ba ni haushin na kasa. Bayan ya tafi Baba yake faɗa min gobe na shirya za mu je inda Saddam yake, iyayen shi ma za su je a yi zama na ƙarshe, na ce to, a raina ina fatan Allah Ya sa ƙarshen wahalata kenan, don wallahi ni ake wahalarwa a wannan lamarin, na matsu na gan ni a ɗakina. Washegari muka shirya, Isma'il ya zo ya ɗauke mu ni da Baba, ina gidan gaba Baba yana baya, da na gaishe ya amsa a daƙile, har muka je ba mu sake magana ba, a can muka tarar da mahaifin Sadam yana jiranmu, aka ba mu wajen zama, aka fito da Sadam, ina kallon shi na san ya sha wuya, don ga duka nan a jikinsa ɓaro-ɓaro, duk ya yi zuru-zuru, don kwanakin da ya yi bai yi shaye-shaye ba duk ya rasa nutsuwarsa, kuma wannan karon da alama ya yi laushi, sai dai yana ta ɓata rai, baban shi yana ganin shi ya fara salati, ya ce "Sadam, yanzu rayuwar da ka zaɓawa kanka kenan ko? Kai fa Musulmi ne ka san ƙaddara indai imaninka ya cika, kana da hankali kuwa za ka dinga bibiyar matar wani?" Sai ya fara hawaye, yana sharewa da sauri, da alama dai bai so ya yi kukan ba fin ƙarfinsa hawayen ya yi, ya ce"Ka yi haƙuri Abba, su ma su yi haƙuri na bar ta in sha Allah". Isma'il ya ce"A'a ban yarda, ƙarya yake yi, wannan yaron tantiri ne, a dai yi maganar da za ta saka na yarda ya bar matata har abada, saboda wallahi ya sake yunƙurin shiga gonata sai na ba shi mamaki". Baban shi ya ce"Ka yi haƙuri Alhaji, shi wannan yaron ba lallai yana cikin hayyacinsa ba, ya shiga matsala ne, ya yi aure, matar ta shi ashe karuwa ce, kuma iyayen bogi ta nuna aka ɗaura aure, rana ɗaya ta bugar da shi da kayan maye, ta kwashe duka kuɗin account ɗin shi, yanzu case ma yana kotu don gidan da yake ciki ma ta siyar da shi, sannan ta zubar da ciki ta saka ɗan tayin a kwali ta ajiye masa, ya shiga tashin hankali sosai, shi ne ya kasa tawakkali ya fara shaye-shayen nan, kuma shi a kullum cewa yake alhakin Sayyada ne, shi ne yake so ta yake masa kuka a haukansa wai ta kashe aurenta ya aure ta, so ne ya ja hakan wallahi, yanzu gidan da ya ce ya bar mata shi kaɗai ne ya rage masa, amma ya ce shi ya riga ya bar mata, kuɗin hayan ɗari shida ne, don ba shi da kuɗi ne ma ya ɗauki dari uku ya ba ta ɗari uku, saboda na rufe ba shi kuɗi na dakatar da shi daga duk kasuwancina, saboda yanayin maye da yake ciki, mun san ya yi kuskure amma ina mai ba ku haƙuri a madadinsa in sha Allah hakan ba zai sake faruwa ba, ni daga nan ma gidan gyaran hali zan kai shi a raba shi da wannan shaye-shayen". Baba ya ce"To shikenan Allah Ya rufa asiri, amma lallai-lallai a sake gargaɗar shi, babu shi babu yarinyar nan, kuma batun gida ta yafe, ya riƙe abun shi, Allah Ya ba da ladan niyya". Baba ya kalli Isma'il ya ce"Ka yi haƙuri, shikenan a bar batun". Ya ce"To ya ba da account a mayar masa da kuɗinsa". Baban Saddam ya ce"Ai ya riga ya ba ta, babu damuwa a bar shi kawai, Allah Ya saka musu albarka". Isma'il ya ce"Babu wata albarka, kuma ai ba rasawa ta yi ba, don haka ku ban account kawai". Baban ya ba shi nashi, ya karɓi yawar Sayyada ta mayar masa da kuɗinsa, aka ce Saddam ya ba shi haƙuri, Sadam ya ce"Ka yi haƙuri in sha Allah ba zai sake faruwa ba, Allah Ya ba ku zaman lafiya". Ba tare da ya kalli inda Sayyada ta ke ba ya ce"Ke ma ki yi haƙuri ki yafe min, cutarwar da na yi miki a haɗuwarmu tun farko har zuwa yanzu, na yaudare ki, na saka ki bijirewa iyayenki, sannan ni ne nake korar wanda ya fito neman aurenki da labarin abin da kika yi min kafin rabuwarmu, ni dai na yafe miki komai". Na ji wani dumm! Na cika da mamakin wai shi ne yake korar manemana dama? Hawaye ya kawo idona kawai yadda na daɗe da zargin Anisa a raina ne ya faɗo min, ashe na cutar da ita, ashe masoyiyata ce ita, ƙoƙari take na samu miji na yi aure, amma shi ne har ta haɗa ni da mijin nunawa sa'a irin Isma'il ban daina fushi da ita ba, bisa zargin a baya ta cutar da ni, ashe duka Saddam ne, kai amma Saddam ya daɗe yana gana min azaba da sunan soyayya. Na ce"Na yafe maka har zuciyata". Na kalli Isma'il na ga ni yake yi wa kallo mai kama da harara. Sannan aka yi nasiha aka ce a yafi juna, kowa ya yafe taron ya watse kowa ya kama gabansa. Da muka dawo gida, Baba ya fita daga mota ni na ƙi fita ina jira mu tattauna, ya ce"Me kike jira?" Na ce"Ka ƙara hakuri". Ya ce"Ai na yi". Na ce"To yaushe zan koma? Zaman wankan ya isa haka". Ya ce"Lokacin da kika so". Na ce"Wai kenan har yanzu fushi kake yi da ni? Ka yarda ina da laifi?" Ya ce"Ba fushi ba ne, kishi ne, kishinki ne kamar ya fasa zuciyata, wannan yaron ya cuce ni fa, ba zan manta da wannan gorin da ya yi min ba". Na ce"Don Allah ka yi haƙuri, kuma na yi maka alƙawarin zan mantar da kai wannan gorin a ranar da na dawo, kai da kake da ni har abada? Ka san tsayin lokacin da za mu shafe tare kafin mutuwar ɗayanmu? Don Allah ka manta". Ya sauke numfashi ya ce"To gobe zan zo mu tafi ko?" Na ce"To ka zo da yamma, saboda akwai abubuwan da zan yi". Ya ce"Ok, Allah Ya kaimu". Na fita, ya ja motar ya tafi, anjima kaɗan na ga alert ya turo min dubu ɗari uku, na tafi gidan Anisa, na dinga ba ta haƙuri har da kukana, na faɗa mata zargin da nake yi mata, ta ce ta yafe min kuma ta yi min uzuri, na ciro kuɗi ta raka ni kasuwa muka yi siyayya, muka wuni muna yin aikin kayan fulawa, wanda zan yi na tsarabar komawa ɗakina. *Masoyan Ustaz next page naku ne, ina can ina fafutukar shawo kan Ruky baby ne* 08028966015 [17/11, 3:51 pm] Sadiya Abdulrazak: 47 USTAZ Zamansu ƙalau da Rauda, suna gamsar da juna, duk da shi yana ta ƙoƙarin ragewa ne saboda kar ya ƙureta ta gaji ta rabu da shi ta shiga uku, don yanzu ya gama yarda idan ba Rakiya ya aura ba samun wacce za ta zauna da shi ta karbi larurar shi abu ne mai wuya, sai Rauda ɗin, siyasa ma ya yi wa kansa faɗa ya rage matsolancin sosai, Alhamdulillah yana wadata gidan da komai yanzu, tun da yana samu daidai gwargwado, idan ya yi tafiyar sati ɗaya ko biyu ya dawo kamar za su cinye juna shi da Rauda, shi yasa suke ƙara jin ƙaunar juna, a nasu ɓangaren dai komai daidai. Ana haka kuma sai ga wata sabuwa ta ɓullo musu, Rakiya ce ta yi karatun ta nutsu, ta ga tun da dai ta rasa mijin aure ne zai hana ta yi maneji da Ustaz? Tun da yana ƙaryar shi hariji ne sai ta yi haƙuri da kishiyar, indai zai biya mata buƙata ranar kwananta, sai ta haƙura da fashin kwana ɗaya, tun da Hausawa sun ce maraina kaɗan zai haƙura da babu, za ta iya ƙin auren shi saboda yana mata, ta je ta auri mara matan kuma ta samu lusari ne, don haka ta faɗawa wacce aka bawa cigiya ta amince da auren, dama wata Hajiya Ladidi ce wacce ake yi wa laƙabi da mai dalilin aure. Ustaz yana zaune ƙalau Umma ta kira shi ta ce ya zo tana son magana da shi, da daddare ya je, bayan sun gaisa take faɗa masa Rakiya ta ce ta amince da auren nan, don haka ya shirya a tura neman aure, Ustaz ya fara salati ya ce"Subhanallah, amma Umma gaskiya dai da an rabu da batunta, ni ina zaune lafiya da matata, kuma ban nemi komai na rasa ba, bi ma'ana dai ba na buƙatar ƙari". Umma ta ce"Ni fa tausayinka nake ji, har ka manta yadda yarinyar nan ta birkice lokaci ɗaya ta dage sai ka sake ta? Kuma dole haka ka sake ta ɗin saboda iyayenta sun ɗaure mata, yanzu ma tsaf wani abu zai gifta rana ɗaya ta ce sai ka sake ta, kuma da ita ga dogara, ai gara ka auri wanda ɗin, ko ba komai gida biyu maganin gobara, ina fargabar ka zo nan gaba ka rasa macen aure, amma ita Rakiya tun da larurarku ɗaya in sha Allah ƙalau za ku zauna, kuma ka ga 'yar talaka ce irinka, don haka ba za ta rainawa ƙoƙarinka ba". Ustaz ya sunkuyar da kai ya ce"Umma wannan ƙarin auren umarni ne ko shawara?" Ta yi masa wani kallo"Umarni ne, idan kuma ban isa ba sai ka faɗa min". Ya fara girgiza kai"Lala-lala wallahi kin isa Umma, shikenan za a san abun yi in sha Allah, amma ina rokon ki taya ni da addu'a, bi ma'ana yadda zan shawo kan ita Rauda ɗin, tun da gaskiya tana cikin mata masu zafafawa, bi ma'ana ta fannin kishi". Umma ta ce"Allah Ya ba ta haƙuri, ya kawo komai cikin sauƙi, kai dai fatana ka zama mai adalci a tsakanin matanka, kowacce a cikinsu da ranarta a gare ka, ka ga ita matarka ta yi maka halacci ta so ka ta zauna da kai, sannan mahaifinta ya yi maka halacci ya ba ka aikin yi, ita kuma Rakiya da za ka aura irin larurarka ce da ita, ka huta wannan raɓe-raɓen da kake yi, to don haka ka riƙe su su biyun da adalci, Allah Ya sanya alkhairi, sai a saka sati uku ma ya isa". Suka yi sallama Ustaz ya tafi, jikinsa a mace ya koma gida, ya kasa ɓoye damuwarsa har sai da Rauda ta fahimta, ta tambaye shi mene ne? Ya ce"Rauda akwai matsala, wallahi ina son ki, ina fargaba da ɗari-ɗarin rabuwa da ke Raudata". Ta ce "Subhanallah me ya faru da kake tunanin za mu rabu?" Ya fara girgiza kai ya janyo ta jikinsa ya ce"Rauda ina sonki, ina son farincikin iyayena, shin za ki iya taimaka min na yi musu biyayya domin na rabauta? Bi ma'ana su ɗaga min ƙafafu na shige aljanna? Kin san a yanzu ni aljannata tana ƙarƙashin ƙafarsu, kafar yadda taki take ƙarƙashin ƙafata, don haka ya zama wajibi na yi musu biyayya matuƙar dai umarnin nasu bai saɓawa shari'a ba". Ta ce"Hakane". Ya ce"To dama, akwai wata yarinya zan ce ko mata ma oho, da ita Umma bi ma'ana mahaifiyata, sai ta ba ni umarnin da na aure ta..." Kafin ya ƙarasa Rauda ta mike daga cinyarsa, ta fara muzurai "Ka aure ta?" Ya janyo hannunta, ta ƙwace ta ce"Kenan dai har yanzu ban ishe ka ba wata kake hange a waje ko?" Ya fara girgiza kai"Subhanallah, Rauda ki ji tsoron Allah, ki sani ni mijinki ne, ba a ɗagawa miji murya, ballantana kuma a ɗaga masa hankali, amma la ba'asa idan don ta ni ne na yafe miki, sai dai ya za ki yi da hukuncin Allah?" Ta banka masa harara ta ce"Ka ma jingine wa'azinka a gefe, don ya daina tasiri a kaina". Ya ce"To shikenan, ki yi haƙuri ki saurare ni, ita fa Rukayya ba sonta nake yi ba, ke ce zaɓina, saboda haka ke ce da riba, Umma ce ta nema min ita tun kafin ki dawo gare ni, bi ma'ana lokacin da muka rabu, to yanzu kuma sai ta ba !ni umarnin da na aure ta lallai-lallai na haɗa ku biyun, don Allah Rauda ki yi min adalci ki bar ni na aure ta, bi ma'ana na cika umarnin mahaifiyata, Rauda duk fa mai saɓawa iyaye ba zai yi albarka ba, idan na ɓalɓalce ke ma ba za ki ji daɗin zama da ni ba". Rauda ta ƙi sauraron shi, ta shige ɗaki, sai da ya yi sati yana lallaɓa ta, kafin ya shawo kanta, ta haƙura ta yarda da auren, nan ma kuma aka zo batun ɗaki, aka dinga tataɓurza ta ce ba za ta zauna mata a gida ba, ƙarshe dai sai zuwa ya yi ya sanarwa mahaifinta, ya ce shi babu ruwan shi a sabgar gidan shi, da ƙyar Rauda ta yarda ya gina wani ɗakin a tsakar gidan, ɗaki ne kamar ciki da falo, amma na cikin ɗan ƙarami ne sosai, shi ne za a mayar kitchen, dama akwai banɗakin tsakar gida. Haka dai ya dinga lallaɓa ta, tana sha masa ƙamshi, taimakon da Allah Ya yi masa shi ne ba ta haɗe masa yanzu duk faɗan da suka yi idan dare ya yi za su jone. Ya bawa Rakiya kuɗin aure dubu ɗari biyu, Rauda kuma ya ba ta dubu ɗari ya ce ta sayi kayan kwalliya,kuma ta karɓa a ranta ta ce ai raba arne da makami ibada ne. Aka ɗaura aure cikin rufin asiri, da rana 'yan'uwanta suka zo suka kawo kayanta, katifa ce babba sai kayan kitchen, don ta ce ta daina yin kayan gado da kujeru don asara suke zame mata, ƙarshe auren ya mutu ta siyar da su a banza, har aka yi jeren aka gama ba su ga idon Rauda ba, don kulle ɗakinta ma ta yi, ko 'yan'uwan Ustaz da suka zo kawo abincin masu jere ba ta bari sun ganta ba, ballantana masu jeren, kishi take yi na gaske a kan mijinta. Da daddare abokan Ustaz guda biyu masu mota suka je suka ɗakko amarya da tsirarun 'yan'uwa, da aka kawo ta haka aka dinga ƙwanƙwasa ƙofar Rauda wai za a ba ta amana, ta ƙi buɗewa, ƙarshe ta kira Ustaz ɗin ta yi masa tass, ta ce idan bai yi musu magana sun shafa mata lafiya ba sai ta fito ta daddana musu na maguzawa, shi ne fa Ustaz ya firgita, don ba ya son fitina, ya kira Rakiya ya ce mata lallai-lallai su rabu da Rauda su ajiye ta a ɗakinta kawai kowa ya kama gabansa, suka tafi suka bar amarya Rakiya zaune, ta tashi ta sake gyara ɗakin komai ya yi mata daidai, ta ɗakko rigar bacci ta saka ta janyo wata leda viva mai cike da kayan mata, ta ɗakko wani abun matsi ta tura, ta baje jarkokik tsumi da zuma, ta samu robar cin abinci ta dinga zuba su ɗaya bayan ɗaya, aka saka gumba, ta zuba madara ta dame su ta ɗaga ta kwankwaɗe, ta mayar da su inda suke, tana jin shigowar Ustaz ta janyo hijjabi ta zumbula. Ɓangaren Rauda ya fara zuwa, ya kira ta a waya ta buɗe masa, ya yi zaton ma za ta ƙi buɗewar, don haka ya shiga da fara'arsa yana faɗin"Raudata Allah Ya yi miki albarka, Allah Ya bar mu tare". Ta harare shi ta ce"Ai dama haka za ka ce, ai ni yanzu ba yarda da maganarka zan yi ba, tun da ka nuna min iyakata". Ya janyo ta jikinsa yana"Haba Raudata, uwargida ran gida, kuma ran Ashir, domin idan kika guje ni na kaɗe". Ta ce"Ba wani nan". Ya ce"Allah kuwa, zan yi kewarki fa". Ta ce"Ni dai je ka, kar ka saka min rai a kan abin da yau ba nawa ba ne". Ya ce"Wallahi naki ne, don yanzu kika ce kina so za ki samu". Ta ce"A'a ba na so, ka je can ka kwana kana bata". Ya yi dariya kawai, ya miƙa mata leda guda ɗaya ya ce"Ga kazarki, ko na zauna na ba ki a baki?" Ta ce"A'a ni dai tafi". Ya tafi yana waiwayenta, ta rufe ƙofar ta zauna ta fara hawaye. Idan Ustaz ya ce ba ya zumuɗin auren ya yi ƙarya, sai dai ya ce ba sonta yake yi ba kawai, amma yana ɗaukin ganin tata jarumar, ko Rauda da ta zama 'yar hannu tana gamsar da shi ne ba wai ya ƙure ƙarfin sha'awarsa ba, don haka zai so a ce ya samu wacce za su kwana suna yi ba tare da tunanin ya shiga hakkinta ba, shiyasa yake jin Rakiya za ta zame masa matar biyan buƙata da samun nutsuwa, ita ma Rauda sai ta huta a ranakun kwanan da ba nata ba. Da sallama ya shiga ɗakin, Rakiya ta amsa, tana kallon shi ta haɗiyi yawu muƙut, abubuwa suka fara motsa mata, ta yi murmushi ta ce"Sannu da zuwa". Ya ce"Yawwa amarya mai araha, wacce ba ta rowar fuskarta". Ta yi yar dariya ta ce "Haba Malam, wannan fa shi ne aurena na shida, to kunyar me zan ji kuma?" Ya ce"Hakane, aurenki na biyar kuma na ƙarshe bi izininllah! Bi ma'ana indai har da gaske rashin gamsuwa ne matsalar dake kashe miki aure to kuwa ki saka a ranki kin zo gidan magani, waraka ta zo bi izininllahi". Ta yi murmushi ta ce"Alhamdulillah, duk da dai ba girin-girin ba ta yi mai". Ya ce"Hmm Ruƙayya kenan, yanzu dai bari na yi wanka, ki yi alwala kafin na fito". Ta tashi ta fita ta zuba ruwa ta kai masa, kafin ya fito ta yi alwala, ya saka jallabiya suka yi sallah raka'a biyu, ya yi musu addu'o'i, yana zare jallabiyar haƙurin Rakiya ya fara ƙarewa, don dama tun daga gida a matse take daurewa kawai take yi, Ustaz ya tura mata keda ya ce ga wannan, sai ki cire kayan shayin, ga kuma kaza, idan akwai ruwan zafi ma zan so a haɗa min shayin, tun safe ban ci komai ba". Rakiya haushi ya fara kama ta, yadda take a uzurce har wani dahuwar shayi yake nema shi, to da tun daga nan gabanta ya fara faɗuwa, ta fara inkarin harijancinsa, ta ce"Ni ba ni da wani ruwan zafi". Ta cire hijjabin ta tashi ta fara yan gyare-gyare a ɗakin, dayake tana da diri sai surarta ta fizgi Ustaz, ya haɗiyi yawu, sai ya tashi yana cewa"Bari dai na yi shaf'i wal wutur, domin ban san yaya za a kaya ba idan aka shiga fagen dagar nan Ya Ruƙayya". Ta ji sam ba za ta iya jurewa ba, nema yake ya ƙure haƙurinta, don haka ta ƙarasa ta janyo shi ya faɗo jikinta, ta shiga sarrafa shi tana faɗin"Haba dai Malam, sai na fito fili na faɗa maka a uzurce nake sannan za ka fahimta?" Ustaz ya ce"Habawa ai ba ko fi ni uzurin nan ba, to amma kin san yana da kyau bawa ya fara da tuna mahaliccinsa, kasancewar na saba sallar dare, ga kuma yau biyu ta haɗu, kar na je na kasa haƙuri ya zamana ban yi sallar ba, shi yasa na ce bari na fara yi, bi ma'ana ba sai na yi ta tsakiyar daren ba, amma dai kar ki ce na shiga hakkinki". Ta sake shi ta ce"To ka yi, amma don Allah ka yi raka'a biyu, wallahi na gaji". Ya ce"Kar ki damu, indai ni ne ai naki ne har sai kin ture". Ta haye katifar ta kwanta, yana idarwa ya kashe hasken ɗakin ya je gare ta, idan ka shiga ɗakin dai ka yi zaton wasu mayunwatan zakuna ne aka haɗa su suke gabza gumurzu, tsakani da Allah Ustaz abun ya yi masa sugar, a cikin matansa dama Rauda ce kawai take yin gyara, ita ma kuma baya-baya ba kamar irin wannan da Rakiya ta yi ba, lallai yau ya tabbata biyu ta haɗu, domin kuwa tun ƙarfe tara ake abu ba ta ce masa ta gaji ba har ƙarfe ɗaya, don gamsuwa bai yi gamsuwar da zai ce wai ya gaji ba, sai dai fa ya fara jin bacci, don haka ya ce mata"Ruƙayya yaya, ba ki gaji ba?" Ta ce"Kai haba wace irin gajiya? Ai ni sai yanzu ma na san an fara lamarin, ƙara dai ko awa biyu ne mu ga abin da hali zai yi". Domin kar ta ga rauninsa sai ya ƙara zage damtse, bayan minti talatin ya ce"Ruƙayya yanzu fa?" Ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Kar dai guduwa na yi ban tsira ba? Wai me kake nufi ne Malam Ashiru? Ba dai ka gaji ba? Yau ga mugun abu ni Rakiya". Ustaz ya ce"Ba fa gajiya na yi ba Ruƙayya, to amma ba za mu yi bacci ba? Gaskiya bacci nake ji wallahi, amma don gajiya ko gamsuwa nima duk ban yi ba, amma wai dama da sai a bawa gangar jiki hakkinta, bi ma'ana bacci". Rakiya ta ce"Tsakani da Allah yau babu lissafin bacci a jadawalin rayuwata, ka rufa min asiri mu cigaba, don wallahi idan ka bar ni yanzu to har gara ma ba ka yi ba". Ya ce"Ke Ruƙayya, Ya Subhanallah, yanzu fa awa huɗu da rabi kenan, to ko goɗiya ce aka tisa ta a gaba zuwa yanzu ai kuwa sai dai ta ce ba ta ƙoshi ba, ba dai ta ce ba a taɓa ta ba". Ta ce"Ni dai ka yi haƙuri ka cigaba, don gaskiya baccin nan sai dai ka haƙura gobe ka fanshe". Ustaz ya cigaba da yaƙi, sai dai fa da gaske bacci yake ji, kuma ya gaji, gajiya ta gangar jiki ba wai ta kashe arna ba, da ƙarfe uku ta yi alarm ɗin wayarsa ya buga ya miƙe da sauri ya ce"Kin ji alarm, da yake ina yin sallah a daidai lokacin nan, bari na yi ko raka'a biyu ce sai kuma na kwanta, wallahi bacci idona har ruwa yake yi". Rakiya ta miƙe ta ruƙo shi ta ce"Ka rufa min asiri Malam, wallahi idan ka bar ni haka haukata ni za ka yi, ya ina yabonka sallah za ka kasa alwala? Daure munƙarasa ladanmu". Ustaz ya ce"La ba'asa, Shikanan mu je, amma dai abun akwai shiga hakki, bi ma'ana yau na shiga hakkin idanuna, ban yi bacci ba har gari zai waye". Da suka koma da ƙyar ya samu ya ƙwaci kansa ƙarfe huɗu, ko wanka bai yi ba bacci ya rafke shi, da alarm ya tashe shi sallar asuba da ƙyar ya tashi, ya yi wanka ya tafi masallaci, da ya dawo ya tarar tana bacci a sallaya, hakan ya ba shi tabbacin ta tashi ta yi sallah, ya koma katifar ya cigaba da bacci. Can cikin bacci ya ji ana shafa shi, ya razana ya buɗe ido, ya ga gari ya waye sosai, ya yi ido huɗu da Rakiya haihuwar uwarta, ya ce"To Allah Ya yi dare gari ya waye kenan". Ta ce"Ƙwarai kuwa, ka fi shayi kuma za mu dosa". Ya tashi zaune ya ce"Wallahi ki saka kayanki idan za ki saka, domin ni nan ba moruwa zan yi ba". Ta ce"Ban gane ba za ka moru ba, anya kuwa kai hariji ne?" Takaici ya kama shi jin za ta mayar da shi rago, ya ce"Cikakke ma kuwa, amma ki tuna da rabona da abinci tun jiya da safe, ko kazar ba ki bari mun ci ba kika farmake ni, hana Ya ke Ruƙayya a dinga sara ana duban bakin gatari mana". Ita ma yunwar take ji, amma wannan abu ya fiye mata abinci, shi yasa ta fara neman shi, ta tsaya tana kallon jikinsa tana haɗiyar yawu, gabansa ya faɗi, a ransa ya ce'Shikenan Umma ta haɗa ni da me gani har hanji, Allah ka dubi bawanka'. Ta fitar da ƙaramin gas ɗinta waje, ta dafa musu shayi, suka ci da biredi, sannan suka ci kazar, ya ce"To ma sha Allah, Alhamdulillah, bari na je mu gaisa da ita Raudatu daga can kuma zan wuce wajen aiki". Ta ce"Haba Malam ya muka yi da kai? Yanzu fa ƙarfe tara, ƙila ma bacci take yi". Ya ce"A'a idan ta tashi da asuba ba ta komawa bacci". Ta ce"Ko dai ka gaji ne" Shi kam ba ya so ta raina shi ta dinga cewa ya gaji, don haka ya ce"Wai me kika mayar da ni ne? Jiyan ma fa gajiyar ɗaurin aure ce, da kuma bacci da nake ji, amma yau za ki sha mamaki". Zai fita ta tare ƙofar ta ce"Na rantse da Allah da ka ƙi ba ni wannan ka fi shayin gara ka hana ni kuɗin cefane". Ustaz ya ce"To fa! Wata sabuwa". Haka ya haƙura aka shiga fagen yaƙi, ƙarfe goma da rabi ya ƙwaci kansa, don Rauda sai kiran wayar shi take. Ya yi wa Rakiya sallama, wacce ta biyo shi har tsakar gidan, ba ta daina shafa shi ba shi kuwa sai mazewa yake, kamar tana shafa dutse, ya ce mata zai yi aiken kayan abinci da cefane, sai da ta ga shigar shi ɗakin Rauda sannan ta koma ɗaki ta kwanta ta fara bacci. Ustaz yana shiga ya ga Rauda ta cika ta batse, ya maze suka gaisa, ta ce"Ai na yi zaton ba za ma ka fita aikin ba yau". Ya ce"A haba, zan fita mana, bacci ne ya ci ƙarfina". Ta ce"Dole ya ci ƙarfinka ai, tun da jiya ba ka runtsa ba, ka samu abin da ba na baka". Ya ce"Haba Rauda, wallahi kina ba ni, sai fa kin yi haƙuri Rauda a hankali za ki saba ai". Ta kanta a jikinsa ta ce"Jiya na kasa bacci saboda kewarka, gaskiya ina buƙatarka, taso mu je ɗaki". Gabansa ya ba da rass, ya ce"Haba dai Raudata, kin san dai yau ba ranar kwananki ba ce, sai fa na yi kwanaki uku zan dawo nan, ki daure kin ji? Kamar yau ne". Ta ce"Gaskiya Ni dai a'a". Ya ce"To ai kuma ba zai yiwu ba tun da ba ke ce da girki ba". Ta ce"Amma ai ba haramun ba ne ko?" Ya ce"E to...amma dai da kin daure ɗin, idan na yi haka tamkar cin fuska ne a gare ta, bi ma'ana ita Ruƙayya ɗin". Ta saki baki"Au kana so ka nuna min a jiyan kawai har ka fara sonta kenan ko? Tun da ga shi ba ka so ka yi mata cin fuska". Sai ta yi fushi ta yi ɗakinta, a ranta kuwa fata take yi ya biyo ta rarrashi, ta saka shi dole ya ba ta hakkinta, shi kuwa Ustaz sai ya yi wa kansa ƙiyamul laili ya fice daga ɗakin da sauri, ya bar gidan yana mitar za su mayar da shi inji". 08028966015 [18/11, 10:52 am] Sadiya Abdulrazak: 48 A wajen aikin ma yana ta tunanin ita Rakiya wace ce ita a nau'in harijai? Bacci sam bai ishe shi ba, haka dai yake ta daurewa, wajen sha biyu da rabi ya kira Rauda a waya, ya ce don Allah ta zubawa Rakiya abinci kafin ya kawo mata yanzu, ta ce ba za ta bayar ba har da rantsuwarta, ga shi babu yaron da zai aika, kuma fargabar komawa gidan yake yi, duk da a yanzu yana jin zai iya yi, to amma ita fa Rakiya abin da za a duba ba ta san zuru ba, yanzu idan ya je ta damƙe shi ya san sai marina, don haks ya ƙi zuwa, sai wajen ƙarfe ɗaya ya aika mata da kayan abincin, amma ya sa a sayi dafaffe a kai mata, bai sani ba ko tana can tana jin yunwa. Rakiya bayan fitarsa ta gyara ɗakinta ta fito tsakar gida ta share tass, ta je ta ci gaba da baccinta, ba ta ma farka ba ballantana ta ji yunwar, sai da ɗan aiken ya zo kawo kayan, ta ci abincin ta yi sallah, ta yi miƙa, sai ta ji ai kawai so take ta ji mijinta a kusa da ita, ta ɗauki waya ta kira shi, suka gaisa ta ce"Me za a dafa maka da rana?" Ya ce"A'a ni ba sai na dawo ba". Ta ce"Haba don Allah, kenan haka za ka zauna da yunwa?" Ya ce"Ai siya nake na ci, kar ki damu babu komai". Ta ce"Amma dai zan yi kewarka gaskiya ka dawo da wuri". Ya ce"In sha Allah". Ya kashe yana hararar wayar, a ransa ya ce'Wannan akwai jaraba. Da yamma ya koma gidan, Rakiya tana jin ƙara buɗe gida ta gane shi ne, tun da ba ta ji alamun Rauda ta fita ba, ta fito tsakar gidan, yana shigowa ta ruga da gudu ta tare shi, Ustaz ya fara murmushin yaƙe, sai dai shi ma nan take ya ji lamura sun fara canza masa, abubuwa suka motsa, ta ja shi suka tafi ɗaki, ita Rauda tun da ta ji dawowar shi ta yi zaton wajenta zai fara zuwa ya ga lafiyarta, amma sai ta ji shiru,don da suka damƙi juna da ƙyar ya yakice ta, shi ma don uzurin sallah ne yasa ta haƙura, ta ce"Don Allah ana idarwa ka dawo". Ya ce"Ai ba sai kin faɗa ba". To da yake ya san hali, ya san me zai faru bai dawo ba sai bayan sallar isha'i, ya fara shiga ɗakin Rauda, sai ɓata rai take yi yana janta da wasa tana fizgewa, ta fara jero masa ƙorafin ya liƙe a wajen matarsa, dama ba gaskiya ba ne da ya ce ba sonta yake yi ba, Ustaz yana ta ƙoƙarin kare kan shi, Rauda tana ƙara botsarewa, ya matsu ya koma can ɗin, saboda ba ya son rashin adalci, tun da ita Rauda ba ita ce da shi ba, ya ce"Ki yi haƙuri Rauda, wannan ne yasa ake bawa mace haƙuri idan za yi mata kishiya, kin ga yanzu dai yunwa nake ji, bari na tafi, idan kwananki ya zo na yi miki alƙawin share miki wannan damuwar da kike ciki". Ta ce"To ka zauna na kawo maka abincin". Don kar ya musa ranta ya ƙara ɓaci sai ya zauna, ta kawo masa abinci ya fara ci, suna fira, a ransa yana tunanin shin iya jiya ne Rakiya ta ƙi ƙoshi saboda zumuɗin auren, ko kuwa kodayaushe a haka take? Idan haka take ai kuwa akwai matsala babba, dole saiya saita ta, don ba zai yiwu ta hana shi ƙiyamul laili ba. Rauda ta yi masa kallon tsanaki ta ce"Sweetheart lafiya kuwa?" Ya sauke numfashi ya ce"A, lafiya lau Alhamdulillah". Ta taɓe baki, a ranta tana fatan Allah Ya sa amaryar ce ya ji ta ba daidai ba. Da ya gama cin abincin ma sai ta ja shi da fira, suna ta yi, ita kuwa Rakiya tuni ta fesa wanka aka yi haɗi irin na jiya aka sha jira kawai take yi ya zo, don ba ta ma saka kaya ba hijjabin kawai ta saka har ƙasa, jin shirun ya yi yawa ya sa ta kira wayar shi, sai da ta ji ƙarar ta tuna ya barta a dakin, ta tashi ta saka takalma ta nufi ɗakin Rauda, ta fara ƙwankwasa tare da sallama, Rauda ta kalle shi ta ce"Amma ban ji an shigo gidan nan ba?" Ustaz da ya gane muryar matarsa ya ce"To kin manta ba mu kaɗai ba ne a gidan?" Sai kuwa ta ɓata rai, ta tashi ta haye cinyarsa, ya ce"Subhanallah, Rauda jirana take yi fa kar abun ya zama cin fuska, bari na je kin ji, haƙurin na kwana uku ne kawai". Ta narke a jikinsa ya ƙi ba shi damar tafiya, jin ya amsa sallamar da take yi ya sa ta buɗe ƙofar ta shigo, ta same su a wannan yanayi, ranta ya ɓaci, amma ta daure ta ce"Sannunku da aiki, baiwar Allah mun wuni lafiya?" Rauda da take ta kallonta tana taɓe baki ta ce"Lafiya ƙalau". A ranta tana mamakin ashe ma babba ce matar tashi, wata mara aji ma, har take kishi a kanta da tunanin kar ta ƙwace mata miji, yanzu wannan ai ba ta hango ta inda za ta ƙwace mata shi ba. Rakiya ta ce"Malam ina ta jiranka ne dama, na ji shirun ya yi yawa". Ustaz ya ce"To Rauda bari na je sai da safe". Rauda ta narke a jikinsa kamar ba ta ji me ya ce ba, Rakiya ta ce"Don Allah ka taso mu tafi, kai fa malami ne, ka san bai dace ka dinga kwaso ranar kwanana kana kai mata ba, ka ji tsoron Allah". Ustaz ya sauke Rauda daga jikinsa, ya tashi, Rakiya ta ce"Ke kuma kin ci bashi wallahi" Ta kama hannun Ustaz suka tafi. Suna shiga ɗaki ta saka sakata, ta yaye hijjabin jikinta, gabansa ya faɗi ya ce"Subhanallah, haba Ruƙayya mene ne haka? Shin ba kya gudun shaiɗanu?" Ta ce"Na yi azkar dai, ni dai mu je don Allah". Sai ya koma da baya, yana haɗe gira ya ce"Ke wai me kika mayar da ni ne? Bi ma'ana me kika ɗauki aure? To ki sani fa ba iya kashe arna ba ne aure akwai fira, akwai kula da juna, yanzu da na dawo sai ki tambaye ni ya aiki? Ya na dawo? Sannan ki kawo min abinci a kai min ruwan wanka da dai sauran abubuwa, kuma bari ki ji na faɗa miki gaskiya, ni idan kina farmakata irin haka zan raina ajinki, ki dinga bari sai na neme ki". Ta ce"To zan yi ƙoƙarin hakan in sha Allah". Ya ce"Yawwa, sannan ni fa ina yin sallar dare, kuma ba zai yiwu a hana ni bacci ba". Ta ce"A'a ta nan dai ka rufa min asiri don Allah". Ya ce"Na rufa miki ni na tona nawa? Kenan na kwana ina yi miki hidima ban runtsa ba na tabbata asararre, to asara mana, kin ga dai na ɗaya ban ribaci lahirata ba, ban yi sallah ba, na biyu kuma zan rasa duniya, tun da zan dinga gyangyaɗi a wajen aiki, ke kuwa da rana za ki sha baccinki, don haka ba zai yiwu ba, dole a yi jadawali a fitar min da hakkina, a ba ni lokacin bacci da ibada". Ta ce"To ka fitar da kanka". Ya ce"Ma sha Allah! Kin ga yanzu dai lokacinki ne, zan kasance da ke daga yanzu takwas da rabi zuwa sha ɗaya da rabi..." "Wallahi ya min kaɗan" Ta katse shi da faɗin haka. [18/11, 5:33 pm] Sadiya Abdulrazak: *LITTAFIN KU YI MANA ADALCI NA KUƊI NE A KAN NAIRA 700, DON ALLAH KAR WACCE TA ZO TA SAKE CE MIN BA TA SAN NA KUƊI BA NE, RAINA ƁACI YAKE, IDAN ZA KI BIYA GA ACCOUNT NAN, IDAN KINA BIN NA BATI KI JIRA SAI AN SAMO A BAKI, DON KIN SAN RASHIN ADALCI NE ZAI SA KI ZO KI CE NA TURO MIKI KO?* 8028966015 Sadiya Abdulrazak opay Shaidar biya ta nan 08028966015 48 A wajen aikin ma yana ta tunanin ita Rakiya wace ce ita a nau'in harijai? Bacci sam bai ishe shi ba, haka dai yake ta daurewa, wajen sha biyu da rabi ya kira Rauda a waya, ya ce don Allah ta zubawa Rakiya abinci kafin ya kawo mata yanzu, ta ce ba za ta bayar ba har da rantsuwarta, ga shi babu yaron da zai aika, kuma fargabar komawa gidan yake yi, duk da a yanzu yana jin zai iya yi, to amma ita fa Rakiya abin da za a duba ba ta san zuru ba, yanzu idan ya je ta damƙe shi ya san sai marina, don haks ya ƙi zuwa, sai wajen ƙarfe ɗaya ya aika mata da kayan abincin, amma ya sa a sayi dafaffe a kai mata, bai sani ba ko tana can tana jin yunwa. Rakiya bayan fitarsa ta gyara ɗakinta ta fito tsakar gida ta share tass, ta je ta ci gaba da baccinta, ba ta ma farka ba ballantana ta ji yunwar, sai da ɗan aiken ya zo kawo kayan, ta ci abincin ta yi sallah, ta yi miƙa, sai ta ji ai kawai so take ta ji mijinta a kusa da ita, ta ɗauki waya ta kira shi, suka gaisa ta ce"Me za a dafa maka da rana?" Ya ce"A'a ni ba sai na dawo ba". Ta ce"Haba don Allah, kenan haka za ka zauna da yunwa?" Ya ce"Ai siya nake na ci, kar ki damu babu komai". Ta ce"Amma dai zan yi kewarka gaskiya ka dawo da wuri". Ya ce"In sha Allah". Ya kashe yana hararar wayar, a ransa ya ce'Wannan akwai jaraba. Da yamma ya koma gidan, Rakiya tana jin ƙara buɗe gida ta gane shi ne, tun da ba ta ji alamun Rauda ta fita ba, ta fito tsakar gidan, yana shigowa ta ruga da gudu ta tare shi, Ustaz ya fara murmushin yaƙe, sai dai shi ma nan take ya ji lamura sun fara canza masa, abubuwa suka motsa, ta ja shi suka tafi ɗaki, ita Rauda tun da ta ji dawowar shi ta yi zaton wajenta zai fara zuwa ya ga lafiyarta, amma sai ta ji shiru,don da suka damƙi juna da ƙyar ya yakice ta, shi ma don uzurin sallah ne yasa ta haƙura, ta ce"Don Allah ana idarwa ka dawo". Ya ce"Ai ba sai kin faɗa ba". To da yake ya san hali, ya san me zai faru bai dawo ba sai bayan sallar isha'i, ya fara shiga ɗakin Rauda, sai ɓata rai take yi yana janta da wasa tana fizgewa, ta fara jero masa ƙorafin ya liƙe a wajen matarsa, dama ba gaskiya ba ne da ya ce ba sonta yake yi ba, Ustaz yana ta ƙoƙarin kare kan shi, Rauda tana ƙara botsarewa, ya matsu ya koma can ɗin, saboda ba ya son rashin adalci, tun da ita Rauda ba ita ce da shi ba, ya ce"Ki yi haƙuri Rauda, wannan ne yasa ake bawa mace haƙuri idan za yi mata kishiya, kin ga yanzu dai yunwa nake ji, bari na tafi, idan kwananki ya zo na yi miki alƙawin share miki wannan damuwar da kike ciki". Ta ce"To ka zauna na kawo maka abincin". Don kar ya musa ranta ya ƙara ɓaci sai ya zauna, ta kawo masa abinci ya fara ci, suna fira, a ransa yana tunanin shin iya jiya ne Rakiya ta ƙi ƙoshi saboda zumuɗin auren, ko kuwa kodayaushe a haka take? Idan haka take ai kuwa akwai matsala babba, dole saiya saita ta, don ba zai yiwu ta hana shi ƙiyamul laili ba. Rauda ta yi masa kallon tsanaki ta ce"Sweetheart lafiya kuwa?" Ya sauke numfashi ya ce"A, lafiya lau Alhamdulillah". Ta taɓe baki, a ranta tana fatan Allah Ya sa amaryar ce ya ji ta ba daidai ba. Da ya gama cin abincin ma sai ta ja shi da fira, suna ta yi, ita kuwa Rakiya tuni ta fesa wanka aka yi haɗi irin na jiya aka sha jira kawai take yi ya zo, don ba ta ma saka kaya ba hijjabin kawai ta saka har ƙasa, jin shirun ya yi yawa ya sa ta kira wayar shi, sai da ta ji ƙarar ta tuna ya barta a dakin, ta tashi ta saka takalma ta nufi ɗakin Rauda, ta fara ƙwankwasa tare da sallama, Rauda ta kalle shi ta ce"Amma ban ji an shigo gidan nan ba?" Ustaz da ya gane muryar matarsa ya ce"To kin manta ba mu kaɗai ba ne a gidan?" Sai kuwa ta ɓata rai, ta tashi ta haye cinyarsa, ya ce"Subhanallah, Rauda jirana take yi fa kar abun ya zama cin fuska, bari na je kin ji, haƙurin na kwana uku ne kawai". Ta narke a jikinsa ya ƙi ba shi damar tafiya, jin ya amsa sallamar da take yi ya sa ta buɗe ƙofar ta shigo, ta same su a wannan yanayi, ranta ya ɓaci, amma ta daure ta ce"Sannunku da aiki, baiwar Allah mun wuni lafiya?" Rauda da take ta kallonta tana taɓe baki ta ce"Lafiya ƙalau". A ranta tana mamakin ashe ma babba ce matar tashi, wata mara aji ma, har take kishi a kanta da tunanin kar ta ƙwace mata miji, yanzu wannan ai ba ta hango ta inda za ta ƙwace mata shi ba. Rakiya ta ce"Malam ina ta jiranka ne dama, na ji shirun ya yi yawa". Ustaz ya ce"To Rauda bari na je sai da safe". Rauda ta narke a jikinsa kamar ba ta ji me ya ce ba, Rakiya ta ce"Don Allah ka taso mu tafi, kai fa malami ne, ka san bai dace ka dinga kwaso ranar kwanana kana kai mata ba, ka ji tsoron Allah". Ustaz ya sauke Rauda daga jikinsa, ya tashi, Rakiya ta ce"Ke kuma kin ci bashi wallahi" Ta kama hannun Ustaz suka tafi. Suna shiga ɗaki ta saka sakata, ta yaye hijjabin jikinta, gabansa ya faɗi ya ce"Subhanallah, haba Ruƙayya mene ne haka? Shin ba kya gudun shaiɗanu?" Ta ce"Na yi azkar dai, ni dai mu je don Allah". Sai ya koma da baya, yana haɗe gira ya ce"Ke wai me kika mayar da ni ne? Bi ma'ana me kika ɗauki aure? To ki sani fa ba iya kashe arna ba ne aure akwai fira, akwai kula da juna, yanzu da na dawo sai ki tambaye ni ya aiki? Ya na dawo? Sannan ki kawo min abinci a kai min ruwan wanka da dai sauran abubuwa, kuma bari ki ji na faɗa miki gaskiya, ni idan kina farmakata irin haka zan raina ajinki, ki dinga bari sai na neme ki". Ta ce"To zan yi ƙoƙarin hakan in sha Allah". Ya ce"Yawwa, sannan ni fa ina yin sallar dare, kuma ba zai yiwu a hana ni bacci ba". Ta ce"A'a ta nan dai ka rufa min asiri don Allah". Ya ce"Na rufa miki ni na tona nawa? Kenan na kwana ina yi miki hidima ban runtsa ba na tabbata asararre, to asara mana, kin ga dai na ɗaya ban ribaci lahirata ba, ban yi sallah ba, na biyu kuma zan rasa duniya, tun da zan dinga gyangyaɗi a wajen aiki, ke kuwa da rana za ki sha baccinki, don haka ba zai yiwu ba, dole a yi jadawali a fitar min da hakkina, a ba ni lokacin bacci da ibada". Ta ce"To ka fitar da kanka". Ya ce"Ma sha Allah! Kin ga yanzu dai lokacinki ne, zan kasance da ke daga yanzu takwas da rabi zuwa sha ɗaya da rabi..." "Wallahi ya min kaɗan" Ta katse shi da faɗin haka, tana yin kicin-kicin da fuska. Ya ce"To ni dai iya haka zan iya, tun da da safe ma za a yi abun nan, ai ba zai yiwu na daina ibada saboda ke ba". Ta ce"Na ji, amma gaskiya da na san kai rago ne tun farko da ban aure la ba wallahi". Ya ce"Alhamdulillah an zo daidai wajen, to ai ni ma da na san jarabarki ta kai ko ibada ki hana da ban aure ki ba wallahi, yanzu ma idan kin ga ba za ki iya ba sai ki yi bayani na sallame ki cikin amince, bi ma'ana na sake ki, ki je ki nemi wanda ya fi ni". Sarai ta san Ustaz ya yi ƙoƙari, ita duk auren da take yi ma ba ta ga wanda ya kai shi jarumta ba, tana yi masa gorin ne kawai don ya yi zuciya ya ƙara ƙaimi, amma babu batun rabuwa, ai ba hauka take yi ba, ita kam yanzu ta ga mijin zama, don haka zama daram". Ta ce"Ka yi haƙuri, yanzu dai ni a uzurce nake". Ta janyo shi ta fara rana shi da kayan jikinsa, ransa duk a ɓace yana jin kamar ma raini ne wannan, sai kace ita ce mijin shi ne matar? Haka aka shiga yaƙin nan, awa uku ana abu ɗaya, Ustaz bacci ya fara fizgar shi, ya ce"Ruƙayya ya ake ciki? Ni dai bacci nake ji, kin san na faɗa miki ba zai yiwu kina hana ni sallah ba". Ta sake ƙanƙame shi ta ce"Ka rufa min asiri Malam, wallahi da saurana, inda jiya ka yi haƙuri mun kwana ƙila yanzu idan aka lissafa da na jiyan sai na gamsu, yanzu hau ka haƙura mu kwana cirr, in sha Allah idan ka yi min na safe shikenan gobe da daddare na yafe maka sai dai ka yi min na awa biyu sai mu yi baccinmu". Ustaz ya ce"Wallahi ba zan kwana ina yi ba, ai ni ba jaki ba ne". Ta ce"Kenan nufinka ni jala ce?" Ya ce"A'a dai ban ce ba, amma wallahi bacci zan yi, a to ba zai yiwu ba". Ya matsa gefe ya juya mata baya, ta ce"Amma dai da asuba za ka ƙarasa". Ya ce"Allah Ya kaimu". Ya tashi ya yi wanka, ya kwanta, bacci mai nauyi ya ɗauke shi, a cikin baccin yana ji tana ta shafa shi, tsoro duk ya kama shi a ransa ya ce'Wannan dai an yi mayya'. Ya yi kamar bai ji ta ba, shi dai ya fi tunanin ba ta yi bacci ba, don duk farkawar da zai yi sai ya ji hannunta a jikinsa. Ya tashi ya yi sallar dare, zai koma bacci ta ce ya taimaka ya yi yanzu, ya ce sai dai idan za ta yafe na asuba, ta ce ta yarda, ya cigaba da yi har asuba, amma da safe ta hana shi fita sai da ya sake yi, ya matsu ya bar ɗakinta ko ya huta, da daddare da ya dawo sai ya shigo mata da karkarwar ƙarya, ya haye katifa yana faɗin"Ruƙayya ban bargo ko zanin gado don Allah". Ya kwanta ya duƙunƙune yana ta girgiza jikinsa, wai karkarwa yake yi. Ta ce"Subhanallah, ba ka da lafiya ne?" Ya ce"Wallahi kuwa, zazzaɓi ne ya rufe ni, kuma na san rashin bacci ne wallahi, dama haka nake idan ba na samun cikakken bacci, wayyo Allah sanyi nake ji". Hankalinta ya tashi, ba wai damuwa ta yi da zazzabin ba, a'a fargabarta ɗaya ya ce ba zai yi mata komai ba saboda ba shi da lafiya, ta ɗakko zanin gado ta lulleɓe shi tana yi masa sannu, a gida ya yi sallar magriba da isha'i saboda ta yarda da gaske ba shi da lafiya, domin ya duba ya ga indai yau ya biye mata ta jigata shi tsotse komai za ta yi, gobe idan zai koma ɗakin Rauda ya rasa abin da zai kai mata, don ita ma tsaf ya gane a uzurcen take da lamarin, haka dai Rakiya ta haƙura a ranar, amma kwana ta yi tana shafa shi. Washegari da ya shiga ɗakin Rauda don yi mata sallamar tafiya kasuwa, ta ce ba ta san zance ba, ai tun da kwananta ya shiga to sai ya ba ta hakkinta, haka ya amince don ya yi adalci, ai kuwa ba ta bari ya bar gidan ba sai wajen sha ɗaya. Da daddare sai ya yi mata na awa biyu ya ce to a yi bacci haka, ta ce sam ita bai ishe ta ba, dayake ita ma ta go shaye-shayen maganinta, saboda tunanin ya yi mata kishiya kar ya fi jin daɗi a can, da ƙyar Ustaz ya samu kansa dab da asuba, ya jigata ko sallar dare bai yi ba, da ya ga take-takenta da safe so take ya ƙara sai kuwa ya yi farat ya ce ai an shiga kwanan Ruƙayya domin shi kwana ɗaya-ɗaya zai dinga yi ba biyu ba, da sauri ma ya fice daga ɗakin, yana shiga ɗakin Rakiya ya tarar za ta shiga wanka, ta yi masa sannu da zuwa, ya ce"Yawwa, dama ban yi muku bayanin kwana ba, gaskiya kwana ɗaiɗai na raba, ta ce"Kana nufin yanzu kwanana ya shiga kenan?" Ya ce"E". Ta washe baki ta ce"Alhamdulillah, dama jiya kwana na yi da kewarka wallahi, ta jefar da zanin tana cewa ka ga kawai na haɗa na yi wankan idan an gama". Ya ce"Subhanallah na faɗo hannun 'yan sari, Ya Allah kai ne ka ƙaddara wanzuwata a tsakanin harijai biyu, sannan ka ba ni ƙarfi irin na hariji ɗaya, Allah Ka taimake ni ka yayewa matana wannan larura ko da ita Ruƙayya ce". SAYYADA Da alama dai cewa da ya yi da ƙyar zan shawo kansa iya fatar baki ne, domin kuwa ana gobe zan koma ɗin da daddare ya kira ni muka daɗe muna yin waya, har na kasa haƙuri na ce"Mai martaba wai ina matarku wacce take sonku?" Ya ce"Au ke ba kya sona ko?" Na ce"Ni wai me yasa ka daina yi min jam'u?" Ya ce"Ai na ga kin fara raina ni, nema kike ki mayar da ni abun wasanki, na daina yi miki magana da jam'u, amma ke kuma dole ki yi min jam'u matuƙar kina so mu shirya". Na ce"Ai yanzu na fara yi ranku ya daɗe, kuskuren baya ma a yafe min tuba nake". Ya yi yar dariya ya ce"Sayyada kina sona?" Na ce"Ni ma ban sani ba". Ya ce"To shikenan, tun da dai ke ba za ki daina wannan yangar ba, sai kin sakko sai kuma ki hau, amma dai na san kina nan kina kewata, ni kuwa ba ruwana da kewar wata tun da ga matata nan kodayaushe a kusa da ni, tana yi min duk yadda nake so". Kishi ya kama ni, na ce"Dama ai ban ce ka yi kewata ba, kamar yadda ni ma ban yi kewarka ba". Ya ce"Idan kika cika baki fa sai na bar ki sai wani satin za ki dawo". Na ce"Don Allah a bar shi ɗin, ni dama ba matsuwa na yi ba ai". Ya ce"Kuma kika nema? Ke fa kika ce za ki dawo". Takaici da kunya ya sa na kashe kiran, na yi masa text massage na ce kar ma ya zo goben don na zan koma ba, na kashe wayata, sai dai kuma murmushi nake yi ina juyi cike da kewar tashi, tsakani da Allah ji nake kamar na janyo goben na gan ni a gidana, cikin ɗakinsa, kan gadonsa, sannan cikin jikin shi. Washegari da safe na je gidan kitso, aka yarfa min shi mai kyau, aka yi min jan lalle, na gama shirya komai na kayana, Mama ma ta gama ba ni abin da za ta ba ni, har mun yi sallama da Baba da zai fita, saboda ina zaton Isma'il zai zo ɗaukata kafin magriba, amma sai na ji shiru har an idar da magriba, ga shi yau ɗin gabaɗaya ma bai kira ni ba, ni ma ban kira shi ba, Mama ta ce"To tafiyar taku ashe sai dare". Na ce"E, ba mamaki yana hanya". Aka idar da sallar isha'i shiru bai zo ba, na shiga ɗaki na kira shi a waya, ya ɗauka yana faɗin"'Yan mata ya aka yi ne?" Na ce"Sai ƙarfe nawa za ka zo ne? Tun rana muka shirya shiru". Ya ce"Ikon Allah, to ke Sayyada kin manta yadda muka yi da ke jiya, kika ce ba ki yi kewata ba, na ce zan bar ki sai wani satin kika ce kin ji, shi ne na bari sai wani satin ɗin". Haushi ya kama ni, na ce"To shikenan, Allah Ya kaimu, ka bari ma sai wata shekarar". Na ajiye wayar ina zaton wasa yake yi min yanzu zai zo, amma sai na ji shiru har ƙarfe goma ta yi, raina duk ya ɓaci, Mama ta ce"Ke Sayyada wannan mijin naki anya zai zo yau kuwa?" Na ce"Ya ce sai gobe, wai zazzaɓi yake yi". Ta ce"Subhanallah, Allah Ya sawaƙe". Na amsa da amin. Can wajen sha biyu na kira shi, bai ɗauka ba, haka na yi kwanan ɓacin rai. Washegari da ya kira ni na ƙi ɗauka, tun yamma na shirya bai zo ba, ganin an idar da sallar isha'i gabana ya fara faɗuwa, na ce to mutumin nan ko da gaske yake ne? Idan don ta ni ce zan iya rabuwa da shi har zuwa satin da ya ce, to amma ba na so Mama ta zargi ba mu shirya ba, don haka na kira shi, na yi sa'a ya ɗauka, na gaishe shi ya amsa yana faɗin"Hajiya Sayyada zaman gida daɗi, ya daren?" Na ɓata rai kamar yana kallona na ce"Na gode da abin da kake yi mini". Kamar bai san me nake nufi ba ya ce"Au wai kati da na saka miki? Haba ai babu komai, hakkina ne". Na ce"Kenan so kake ka nunawa iyayena ba ka huce ba shi yasa ba za ka zo mu tafi ba ko?" Ya yi 'yar dariya ya ce"Ban da rigima irin taki ke fa kika ce sai shekara, ni fa har ba fara lissafi, ke har na yi wa Hajiyata albishir ɗin za ta same ni babu sharing da ke na shekara ɗaya, sai murna take yi, har ma ta ce za ta zo ta kawo miki kyauta har gida". Na ce"Ni dai don Allah ka zo mu tafi, ba na son haka". Ya ce"Kin yi kewata?" Na yi shiru raina yana ƙara ɓaci. Ya ce"Wallahi sai kin ce na yi kewarku mai martaba sannan zan zo mu tafi, idan ba haka ba sai kin yi sati cif". Na ƙi magana, kamar na yanke kiran, sai dai na san indai na sake kwana yau a gida dole iyayena su ce da matsala. Ya ce"Shikanan sai da safe, Hajiya tana jirana zan yi mata tausa". Kamar zan yi kuka na ce"Na yi kewarku mai martaba". Ya ce"Da gaske? Kuma sosai?" Na katse wayar. Ƙarfe tara saura sai ga sallamar shi, na sauke ajiyar zuciya, Abiy ya yi bacci don haka Mama ta ce mu rabu da shi, daga baya a kawo shi, na goya Daddy ya ɗaukar mana kayan namu muka shiga mota muka tafi. Mun fara tafiya ya kunna rediyon motar, kawai sai ji na yi muryata tana ta maimaita 'Na yi kewarku mai martaba' Ya dinga dariya yana cewa"Ai na ji kin yi kewata, ki haƙura ki yi shiru haka". Shi kuwa recording sai yi yake, takaici ya hana ni magana, na ji kamar zan yi kuka, tabbas wannan tsiyar da Saddam ya yi min ta saka farashin jan ajina ya ruguje rugu-rugu, bai kashe ba har sai da muka ƙarasa gidan. Mun fita daga motar, ya ce na shiga mu gaisa da Hajiya don ta san na dawo. Na ce"Amma idan ka faɗa mata ma ai ya wadatar, kuma ita ya kamata ta zo ta yi min sannu da zuwa". Ya ce"A'a ba ki so gaskiya ba, ko ma dai hakan ne, ni na ba ki umarnin ki je ki gaishe ta". Ban yi musu ba muka shiga, tana ganinmu ta taso da fara'arta ta tare ni kamar za ta rungume tana faɗin"Oyoyo Daddy, ɗana ya dawo, sannunku da dawowa, kunto min shi na gan shi". Na kunto shi na ba ta. Ta shiga ririta shi tana faɗin"Ma sha Allah, yaro ya yi wayo, wallahi har mafarkinsa nake yi, sai dai idan ban kwanta ba". Sai kuma ta fara kuka. Isma'il ya ce"Yi haƙuri Hajiya, mene ne kuma abun kuka?" Ta ce"Kukan farinciki ne wallahi, ashe zan ga jininku mai martaba? To ni dai ba ni da rabon ganin nawa, don Allah ku taimaka ku sa yaran nan su kalle ni kamar uwa, su ce min Umma ko zan ji sanyi a raina, jinsa nake kamar ɗana". Ta rushe da kuka. Ya tashi ya koma kusa da ita ya rungume, kishi ya motsa min, na tashi ina faɗin"Ni dai bacci nake ji, sai da safe". Na ƙarasa sashena, na buɗe na shiga, ko'ina fess yake, don yana gyarawa, na shiga ɗakina na yi wanka, na fito ina shiryawa sai ga shi da yaron, ya zauna a bakin gadon yana faɗin"Wallahi yau Hajiya ta ba ni tausayi, sai da ta saka ni hawaye, Ya Allah duk macen da ba ta haihu ba take nema, Allah Ya ba ta haihuwar yara masu albarka". Na ce"Abun da tausayi kam, Allah Ya ba ta wani rabon madadin yaran". Ya ce"Amin" A ransa kuma yana ayyana dole idan Sayyada ta ƙara haihuwa ya bawa Hajiya ɗan ta shayar da shi ita ma ta samu mai kiranta uwa. Ya tashi yana cewa"To ni zan wuce, ina jiranki idan kin gama". Zai tafi da ɗan, na ce"Ajiye shi, zan canza masa pampers". Ya ajiye shi ya tafi, yana fita na murzawa ƙofata key, a fili na furta "Ba dai ni ce na yi kewarka ba? Kuma har za ka rungumi matarka a gabana? Da ni kake zancen". 08028966015 [19/11, 3:46 pm] Sadiya Abdulrazak: 49 Na gama komai na kwanta na yi mana addu'a ni da ɗana. Mai martaba yana can yana jirana, da ya ji shirun ya yi yawa sai ya fara yi min plashing, yana ta yi babu ƙaƙƙautawa, ni kuwa na kashe wayar, sai ga shi yana buga ƙofata tare da kirana da murya mai sanyi "Sayyada, Sayyadata". Na yi shiru kamar ban ji ba. "Buɗe mana Sayyada, da wani sabon salon kika dawo kenan ko? Ba za ki buɗe ba?" Na yi ƙirmisisi, ya sanyaya murya ya ce"Wani abun ne ya faru? Buɗe mu yi magana kin ji". Na ki buɗewa, har dai ya fusata "Ke ba magana nake yi miki ba? Umarni nake ba ki ba lallaɓa ki ba, ki buɗe ƙofar nan!". Sai ma na yi juyi ba ni da niyyar buɗewar. Ya ce"Shikanan, na tafi wajen matata, ai gida biyu maganin gobara". Wani abu ya daki zuciyata, na tashi zaune, ni fa ko me za mu yi ba na so ya dinga bari wani yana fahimtar halin da muke ciki, ina jin ƙarar buɗe falon na sauka daga gadon da sauri na fita da ɗan guduna, har ya fice na bi shi, ya yi kamar bai gan ni ba ya nufi sashen Hajiya, na ce"To ba ga shi na buɗe ba?" Ya ce"Ba na buƙata". Na yi gudu na riƙe shi ƙam, ina faɗin"Ba na son haka, ai na buɗe ko?" Ya ce"Sayyada kar ki ga na sake miki fa ki ɗauka na janye batun sai kin lallaɓa ni". Na ce"Na ji, mu je sai na lallaɓa ka ɗin". Ya tsaya yana yi min kallo mai kama da harara, na kalli gefe ina ɓata rai, ganin ba zai ce komai ba sai na ja hannunsa muka fara tafiya, muka koma ɗakin, na rufe na wuce da shi ɗakinsa, muka shiga, na zauna a bakin gado ina ɓata rai, sai ya yi murmushi ya zauna a kusa da ni yana cewa "Sayyadata sarkin kishi, ashe shi yasa aka ce mai mata biyu ɗan gata, yanzu da ke kaɗai ce yau sai abin da na gani ko?" Na ce"Ni fa kawai idan ka san za ka dinga naniƙar matarka to ka daina ja na wajenta na gani". Ya ce"Inyee, au don na taɓa matata shi ne matsalar dama? To ke yanzu da kika janyo ni ɗaki ba don ki taɓa ni ba ne? Yau ga ikon Allah ki samu kace da mijinta ki shigo tsakiya ita ba ta yi kishi da ke ba, sai ke ce za ki yi kishi da ita?" Na ce"Idan ta yi ɗin ai ba faɗa maka za ta yi ba". Ya jinjina kai "Na lura da wani rashin kunya kika dawo, wanda kika daina yi a baya, don haka ki yi ke kaɗai, kin ga tafiyata, mun tafi wajen matarmu ta kula da mu". Ya yi hanyar fita na riƙo shi, ya haɗe rai "Sake ni, ba za mu iya wannan kumburin da kike yi mana ba, ba za mu ɗauka ba". Na ce"To ka yi haƙuri na daina". Ya ce"Ki yi jam'u da kirari tukuna". Na ce"Ku yi haƙuri ranku ya daɗe". Ya ce"Ki yi min kirari idan ba haka ba ko ban tafi ba na juya miki baya, ko na zuge tazugena don na lura abin da kike yiwa kenan". Na ce"Na ji a zuge ɗin". Ya ce"Ok". Na hau gadon na kwanta, shi kuma ya kashe hasken ɗakin ya kwanta ya juya bayan kamar yadda ya ce. Sai dai babu daɗewa ya ce"Sayyada". "Na'am" Na amsa ina ƙara matsawa gefe. Ya ce"Ba ki yi kewata ba ko?" Na ce"Ai kai ne ba ka yi kewata ba, shi yasa kake ta ja min rai". Ya ce"To bari, ɗan matso ki ji". Na ce"Bacci nake ji, ba abin da zan ji". Ya ce"Sayyada ki fa daina mazewa, na san cike kike da kewata, ki matso na ba ki hakkinki". "Ai tun da hakkina ne na yafe maka, duk sanda na nema sai a ba ni". Ya yi dariya ya matso ya janyo ni ya ce"Kin rantse sai ni ne zan dinga binki da hakkinki ke ba za ki nema ba ko? Ke ce kawai kike ruguza sarautata Sayyada". Na ce"To ai ko sarkin gasken ma idan aka zo wannan batun ajiye sarautar yake yi ballantana kai taka-haye". Ya ce"Yau kuwa za ki ga taka-haye, idan ba ki fara yi min jam'u da kirari ba sai gobe zan saurara miki". Na ce"Allah Ya huci zuciyarku, ƙarya nake 'yar talakawa". Muka yi dariya a tare, ya kwashe ni muka shilla duniyar masoya. Faɗin nutsuwar da muka samu ɓata baki ne, wannan daren ya fi kowane dare a tsayin zamanmu samun nutsuwa, don na gyara kaina sosai, ko daren farkona a gidan Sadam albarka, mai martaba ya yaba ya ƙara, da safe ya ba ni tukuici mai nauyi, sannan ya ce na yi masa alƙawarin ba zan yi planing ba, saboda yana son haihuwa da yawa, yana so ya tara yara tun da girma yake, na yi masa alƙawari kuma na amince har zuciyata, tare da yaƙinin ko yau na samu wani cikin ba zan damu ba. Na fito da kayan tsarabar da na zo da shi, na warewa Hajiya Halima nata na ce masa ga shi idan ya shiga ya miƙa mata. Ya zabga min harara ya ce"Ni ɗan aikenki ne? Sai ki bari idan Dauda ya dawo, ko kuma idan Daddy ya yi ƙafa ki aike shi". Na ce"Ni fa ba haka ba, gani na yi ai za ka shiga dole". Ya ce"To ke ma dole za ki shiga ki gaishe ta ki kai mata, idan ba haka ba ki bar shi ba ta so". Har zai fita ya dawo ya ce"Zan faɗa mata indai ba da kanki kika kai mata ba kar ta karɓa, kuma idan ba ki ba ta tsarabar nan ba na san zaman da zan yi da ke". Wani tunani na yi, idan har da gaske zai faɗa mata na san ba za ta taɓa barin ƙofar nan ƙalau ba, sai ta san tuggun da ta haɗa min, don haka na tashi da sauri na ce"To na ji mu je tare sai na ba ta". Na ɗauki kayan, shi kuma ya ɗauki Daddy muka fita, muna tafe yake cewa"Wallahi Sayyada ina tausayin matata, rashin haihuwa ƙaddara ce mai zafi, sai mutum ya jure, shiyasa nake ta addu'ar Allah Ya sanyaya mata ranta, sannan don Allah ki taya ni ganin ba mu yi wani abu da zai sosa ranta ba a kan wannan yaron". Na ce"In sha Allah zan yi iya yina". Ya ce"Ina so ki dinga kai mata shi duk safiya, ko kuma idan za ki yi wani abun, ya zamana yana da ɗaku biyu dai, yadda za ta dinga jin daɗi da ganin ita ma tana da ɗa". Na amsa da to, muka shiga ɗakin, tana cikin ɗaki, ya shiga ya kira ta, sai ga su sun fito tana riƙe da ɗan tana ta murmushi, na gaishe ta, ta amsa tana cewa"Ya ɗana ya kwana?" Na ce"Lafiya ƙalau" Na ba ta tsarabar na tashi zan tafi, tun kafin ya fara rungume ta raina ɓaci. Amma kawai sai na ji ta fashe da kuka, kafin na juye ta ce"Sayyada ina neman alfarma, mai martaba ku saka baki don Allah ko zuciyata za ta yi sanyi". Duk sai ya ruɗe yana tambayar me take so, na dawo na zauna, ta ce"Ina son yara tun ina yarinya, sai ga shi Allah bai ƙaddara ina cikin mata masu haihuwa ba, mai martaba duk da dai ɗanku nawa ne amma akwai bambanci indai Sayyada ba ta buɗe zuciyarta ta zauna da ni lafiya ƙalau kuma da zuciya ɗaya ba". A raina na ce'An zo wajen'. Mai martaba ya ce"Hajiya Sayyada ba ta da matsala fa, kuma ai ga shi kuna zaune lafiya, yanzu mene ne buƙatarki?" Ta ce"Ina so ne mu ƙara samun kusanci sosai, ta ɗauki Kamar yaya ba kishiya ba, sannan wannan yaron ya dinga kawo min shi don Allah, kuma ta dinga zuwa nan tana zama muna wuni ko kuma ni na dinga zuwar nata, alfarma za ki yi min Sayyada, saboda soyayyar wannan yaron da ta kama ni, don Allah ki nuna masa ni ma uwarsa ce". Na ce"In sha Allah zan dinga kawo miki shi, Allah Ya huci zuciyarki". Tana shassheƙar kuka ta ce"Na gode sosai Sayyada, Allah Ya haɗa kanmu". Mai martaba ya ce"Wannan yaron da duk wanda za a aifa ke ma ɗanki ne ai, haihuwarsa ce kawai ba ki yi ba, kina da iko da su". Ta ce"Na gode ranku ya daɗe, Allah Ya cigaba da dafa muku, Ya biya muku buƙatunku na Alkhairi". Na tashi na ce"To ni zan je na ƙarasa aiki, tun da ban faɗawa mai taya ni ɗin na dawo ba, sai ka dawo Allah Ya tsare". Ya amsa da Amin, na fita na koma sashena, na zauna ina tunani, ni dai ba zai taɓa yiwuwa na dinga zuwa sashenta na zauna ba, ƙarya ne wannan, sai dai ita ta zo nawa sashen idan za ta iya, ɗa dai tun da na san babu yadda zan yi na nuna masa ba lallai da gaske take son shi ba to zan dinga ba ta shi idan ta zo ta karɓa, don ba zan kai mata ba, tun da ba neman kai nake yi da shi ba. Mai martaba ya fita babu jimawa sai ga mai aikinta ta dawo da yaron yana ta kuka, na karɓe shi gabana yana faɗuwa, ta ce"Kuka yake yi ina ga yunwa yake ji, ta ce idan ta sha a dawo da shi". Na ce"To" na karɓe shi ina jijjiga shi, na fara shayar da shi, sai ya yi bacci, ko da ya tashi ma ban mayar da shi ba, don ni ma ina son ganin abuna. Da ya dawo ya fara tsayawa a ɓangarenta, sai ga shi ya shigo min ransa a ɓace, na tare shi da tambayar lafiya? Ya ce"Sayyada ba na son fitina fa, ni gaskiya indai kika ce fuska biyu za ki dinga yi min to za mu dinga samun matsala da ke". Yana faɗin haka na san ta haɗa min wani tuggun ne, na ce"Me na yi maka?" Ya ce"Ɗazu da ke aka zauna aka yi magana da Hajiya a kan yaron nan, me yasa ba ki ce min ba ki amince ba?" Na ce"Me na yi wanda ya nuna ban amince ba? Me na yi mata?" Ya ce"Ta ce min ina tafiya kika zo kika ɗauki yaron, kuma ta zo da rana za ta ɗauke shi kika hana". Na yi shiru na kasa magana. Ya ce"To ba na son haka, ba zan lamunta ba". Na ce"To, ka yi haƙuri". Jikina a sanyaye na kawo masa abinci, na zauna na shiga ba shi a baki irin yadda yake so, sai dai na ƙi sakin fuskata saboda zuciyata babu daɗi, shi da kansa ya lura da hakan ya ce"Sayyada, ba na so na dinga yi miki faɗa, ki daina don Allah, ki dinga kiyayewa, idan kika lura matar nan abar tausayi ce, ko yaya kika nuna ba ta isa da ɗan nan ba kuma na yi shiru ban tsawatar ba, za ta ga kamar na koma ɓangarenki ne gabaɗaya saboda kin haihu ita ba ta haihu ba". Na ce"To". Ya ce"Ban gane to ba, magana za ki yi ki faɗi dalilinki na yi mata haka". Na ce"Ko na faɗa ba za ka fahimta ba, tun da ka yarda da ita, ita ce mai gaskiyar da komai ta faɗa daidai ne, babu buƙatar ka ji ta bakina ko kuma ka yi bincike". Zai yi magana na ce"Don Allah ba sai ka ce komai ba, Shikanan na ɗauki laifin ka yi haƙuri, ba dai sashenta kake so na dinga zuwa ba kuma na dinga kai mata ɗa? Zan je in sha Allah, idan ka ce na bar mata ɗan ma sai na bar mata, ai dai ba a mahaifiya biyu sai dai uwa biyu". Ya ce"Kina da rigima fa, shikenan a bar zancen". Muka bar zancen, yau ma muka yi kwanan farinciki kamar jiya. Washegari wajen ƙarfe goma mun goma komai, na ɗauki Daddy na tafi ɓangaren Hajiya, ba ta falo tana cikin ɗaki, mai taya ta aiki ta leƙa ta faɗa mata na zo, amma matar nan ta ƙi fitowa, na ba ta minti talatin ina zaman jira, goma da rabi tana yi na tashi na tafi, na kira shi a waya na yi masa ya aiki, ya ce"Lafiya lau ya mutanen gidan? Kin kaiwa Hajiya ɗanta?" Na ce"Na je, ba ta falo kuma na yi jiran minti talatin ba ta fito ba, don haka na tafi". Ya ce"Ƙila bacci take yi, don Allah anjima ki koma". Na amsa da to, na bi umarninsa da yamma ma na leƙa, amma ina shiga na kunna recording a wayata, lokacin tana falo tana tsifa, na zauna na gaishe ta fuska babu yabo babu fallasa, ta amsa a daƙile, na ce "Ga Daddy na kawo miki ku gaisa". Ta ce"Ai kin ga tsifa nake yi ko? Ko ki jira ko kuma ki kwashe shi ku koma inda kika fito". Na ce"To mun gode". Ta ce"Umma ta gaida Assha, gayyar tsiya, mai suffar munafukai, ni da Isma'il mutu-ka-raba, ko duniya za ki haifa masa ba zai juya min baya ba, domin tun da na riga ki kwana sai na riga ki tashi!". Na ce"Hmm, to a yi dai mu gani". Na fice daga ɗakin, na kashe recording ɗin. A ƙa'ida idan ya dawo wacce ba ita ce da girki ba ɗakinta yake fara zuwa, idan aka gaisa sai ya je ɗakin mai girki, don haka yau ɗakin Sayyada ya kamata ya fara zuwa, amma da yake Hajiya Halima ta shirya abun yi, sai ta tare shi tun daga tsakar gida, tana share ƙwalla tana yi masa sannu da zuwa. Hankalinsa ya fara tashi, shi sam ba ya so ya ga wani nashi a cikin damuwa, ya ce"Hajiya lafiya? Mene ne ya faru?" Ta ce"Don Allah wannan zumunci da kuke son ƙullawa a bar shi, ba dole ba ne tun da matsala zai zama, yau matarku ta ci mutuncina, ta yi min gorin haihuwa saboda na je ɗaukar ɗan da ka ce nawa ne, ko ku da kuka ajiye ni ba ku yi min gorin haihuwa ba sai ita? Idan ba dama ni kawai zan tafi gidanmu, rashin haihuwa wani ciwo ne a zuciyata, ba zan yarda a dinga fama mini shi ba, iyayena suna sona, auren ana yin shi ne don a haihu, tun da ba zan haihu ba ni na haƙura, ba zai yiwu ƙanwar ƙanwata ta dinga cin mutuncina ba, ku gafarce ni mai martaba ni zan tafi". Ta rushe da kuka Ya rungume ta a jikinsa yana buga bayanta a hankali, ransa ya yi matuƙar ɓaci, sai da ta tsagaita da kukan ya kama hannunta ya kai ta ɗaki, ya ce"Ki yi haƙuri Hajiyata, ina zuwa". Ya fita ya yi sashen Sayyada. Ina tsaye goye da Daddy wanda yake ta kuka na rigimar bacci, ya faɗo ɗakin, ina kallon shi na ga a fusace yake, gabana ya faɗi, kuma ban kawo komai ba sai ita ɗin, tun da ni dai yanzu ita ce ƙaddarata ta gidan aure, na ce"Sannu da zuwa". Ya ɗaga min hannu ya ce"Dakata! Ki riƙe sannu da zuwanki matata ta yi min". Na cigaba da zagaye a falon ina jijjiga ɗana. Ya ce"Wato ke Sayyada nema kike ki zama fitina a cikin gidan nan? Duk yadda na so ku zauna lafiya kin ƙi". Na ce"Don Allah me na yi? Ka dinga jin ta bakina kafin ya yanke min hukunci, Kodayake dama akuyata ta yi kuka a wajenka ai, me ta ce maka na yi?" Ya ce"Kar ki sake ki yi min rashin kunya, saboda wulaƙanci abin naki har ya kai ki je ki ciwa matata mutunci, kuma saboda jahilci har ma da gorin haihuwa? Haihuwar ke kika ba wa kanki? Ko an faɗa miki Allah ba Ya sonta ne ke ya fi so da ya ba ki bai ba ta ba?" Na ce"Wallahi ban yi mata gori ba, kuma ni ba jahila ba ce, ita ce jahila da ta manta za mu je madakata za a yi mana hisabi". Ya zaburo kamar zai dake ni ya ce"Yi min shiru! Mara kunya kawai, ba dai taƙamarki yaron nan ba? Da shi kike ɗaga mata kai ai ko? To zan iya karɓar shi na ba ta, ta riƙe shi kuma har abada, ai ɗana ne ina da iko da shi ba ke kaɗai kika haife shi ba". Na zauna na fashe da kuka mai tsanani, na kunce goyon na baje shi a kujera na ce"Ga shi nan ka ba ta shi tun yanzu". Ai kuwa ya ɗauke shi ya fita, kukana ya tsananta, na yi iya yina, sannan na tafi ɗaki na haɗa jakar kayana na ɗauki kuɗin mota na fito, zan fita shi kuma ya zo tafiya masallaci, ya kalle ni rai a ɓace ya ce"Koma ɗakinki!" Na ce"Gidanmu zan tafi saboda ba zan iya ba, ka zauna da matarka ita kaɗai zai fi maka". Ya ce"Ai dama ban ce ba za ki tafi ba, ko bari gobe da safe ko da asuba ne sai ki tafi, amma yau dai ba za ki bar gidan nan ba". Na tsaya na ƙi komawa, a gabana suka tafi masallaci tare da mai gadin, na gwada buɗe ƙofar ta ƙi buɗewa don an kulle ta da mukulli, na juya na koma, sai kuwa na ga Hajiya tana leƙenmu ta windo, ta yi min wani makirin murmushi ta yi maganar fa ban jiyo me ta ce ba, saboda mun yi nesa, na koma ɗaki na zauna ina ta kuka, na kira Mama a waya na sanar da ita, sai kuwa ta ce ko me zai faru kar na sake na dawo gida da sunan yaji, ai dama ita rayuwa iya ruwa ne fid da kai, don haka na dan yadda zan yi da kishiyata. Haka na haƙura, da ya dawo daga masallaci ya zo ya shiga ɗakin Abiy inda kayan yaron yake, ya ɗauki kayan shi ya fita, yana ta fushi kamar bai taɓa dariya ba, haka na kwana cike da damuwa, don ma na rage tsayin daren da sallah. Washegari da safe wajen ƙarfe shida sai ga shi ya shigo da yaron a hannu, ya ajiye shi a gadon da nake kwance, ya ce"Ga shi nan, Hajiyar zazzaɓi take yi ne, amma tana jin sauƙi zan mayar mata da ɗanta, idan kuma za ki tafi to kar ki tafi da shi, ki faɗa min na zo na ɗauke shi". Na yi banza da shi, ya ce"Magana nake yi miki". Nan ma dai ban kula shi ba, ya fice daga ɗakin. Dama yau na ranar kwananta ne don haka ban sake ganin shi ba ma, washegari ma sai dare da ya dawo, shi ma ɗakinta ya fara sauka sai wajen ƙarfe goma ya zo ɗakina, lokacin har na yi shirin bacci, kishi ne ya hana ni baccin ina jira na ga zai zo ko zai kai mata kwanana ne? Bai neme ni ba, ni ma na kama kaina ban sake zuwa ɗakin shi ba, idan na gan shi dai ina gaishe shi, domin kuwa sai ranar kwanana ta zo ta wuce ban gan shi ba ma, zan bar masa abinci dai kuma na ga yana ci. Sai da aka yi sati ɗaya a haka, wataran kwanana ya zagayo sai ya fara yi min wannan plashing ɗin, na kashe wayata, sai ga shi ya zo ɗakin nawa, ya ce"Wato Sayyada gaba kike yi da ni ko?" Na ce"Ni ba gaba nake yi ba, idan mun haɗu ai muna gaisawa ko?" Ya ce"To amma ai da ba haka kike yi min ba, kin fi mu yi ta zama a haka kenan?" Na ce"Tun da haka ka zaɓa ba". Ya ce"To ya isa kar ki yi min rashin kunya, tashi mu je na duba ki". Ban yi musu ba na tashi na bi shi, ya dinga ja na da fira na yi banza da shi, sai ya kama kan shi shi ma ya shiga neman abin da yake buƙata, ai kuwa na yi masa kwance tamkar satin farko na aurenmu, ran shi ya ɓaci sai haƙura ma ya yi ya ce na tafi ya fasa, ban tafin ba, na kunna wayata, na kunna recording ɗin da na so ya tsaya ya ji a ranar da abun ya faru ya ƙi, ai kuwa ya yi shiru yana saurara, yana ƙarewa na ɗauki wayata na tashi zan bar ɗakin, sai ya riƙo ni, ya ce"Sayyada dawo mu yi magana". To har ga Allah ni ma na gaji da wannan zaman namu mara daɗi, don haka ban yi musu ba na dawo na zauna, ya ce"Da gaske wannan ba editing ba ne?" Na ce"Idan kana kokonto ba sai ka yarda ba ai, da sannu lokaci zai tantance maka". Jikinsa ya yi sanyi, ya gane muryar Hajiya tabbas, kuma abin da ya fi tsaya masa a rai wai har ta iya kiran sunan shi gatsal Isma'il babu mai martaba? Ya janyo ni jikinsa ya ce"Ki yi haƙuri Sayyada, ai ba ki faɗa min yadda aka yi ba". Na ce"Ai ba ka ba ni dama ba". Ya ce"Ki yafe min, kaidinku mata ya fi na shaiɗan". Na ce"Na wasu matan dai". Ya ce"Don Allah ki yi haƙuri, kuma na gode da ba ki biye min kin tafi ba, yanzu kam na tabbata ƙarya zazzaɓi ta yi don kar ta kula da yaron nan, lallai lamarin duniya da ban mamaki yake". Na ce"Ka manta, ya wuce in sha Allah! Yanzu ka ba ni hakkina ba zan yi maka irin na ɗazu ba". Ya ce"Yi haƙuri sai gobe, jikina ya yi sanyi". Na ce"Ai ɗumamaka zan yi". Ban hakura ba sai da na saka shi ya manta da komai a wannan daren, muka shirya kamar ba a yi ba. 08028966015 [21/11, 7:32 am] Sadiya Abdulrazak: 50 Washegari har ya tafi wajen aiki sai ya kira ni a waya ya ce na tura masa recording ɗin nan, na tura masa, ban san dai yadda suka ƙare ba, da daddare ya dawo tare da Abiy, washegari na ce ya kai ni gidansu, muka je muka wuni a can, ni dai tun da na zo gidan ban taɓa ganin ko sabga ake yi Hajiya Halima ta je gidansu Isma'il ba, abun har mamaki yake ba ni. Haka muka cigaba da rayuwa, sai Hajiya ta tsiri zuwa ɗakina, za ta zo ta zauna, ni dai daga gaisawa ba na ce mata komai, sannan ba ta cewa ma na ba ta ɗana, ban san dai me yake kawo ta ba, shi yasa nake zama na kafa na tsare, da aka kwana biyu ana yin haka sai ta daina zuwa, muna ta zaman lafiya da Mai martaba, sai idan ya so tsiyar shi sai ya ce dole na yi masa jam'u, ya fi yi min haka idan ya ga ina so ya bar ni fita unguwa, idan kuma ya so barkwnaci sai ya ce ni ma sarauniya ce, ya wuni yana yi min jam'u. Babu kalar gatan da ba ya yi mana ni da yarana, wanda ban ga alamar zai bambanta su ba, sai dai ko a gaba, tun da dai naka naka ne, shekarar ɗana ɗaya na samu wani cikin, sai dai wannan me laulayi ne ba kamar sauran cikina ba, na dinga 'yan cututtuka, don haka dole Hajiya ta san halin da nake ciki tun da wuri, ai kuwa ta kasa ɓoye baƙincikinta, makirci ya dawo sabo, wataran ya dawo daga aiki kawai ta saka shi a gaba da kuka wai na yi mata gorin haihuwa, ita ta gaji ba za ta iya zama da ni ba, ko ya canza min gida ta daina jin gorina ko kuma ya sake ta kawai, sam bai yarda da ita ba, tun da dai yanzu ya gane tana yi min sharri, ya taho ɓangarena ya ce na taso mu je ɓangarenta, ina kwance jiki duk kasala haka na tashi, mun zo wucewa ta window muka ji muryarta tana waya, ya dakata ya kasa kunne, ni ma na tsaya, dariya take yi tana faɗin"Yanzu na sake haɗa su ai, kuma na faɗa masa ko dai ya raba mana gida ko ya sake ni, haba ban taɓa tsanar wani yaro ba a rayuwata kamar wannan ɗan nashi mai ƙaton kai, yanzu wai ta sake samun wani cikin, saboda zalama konika ma za ta yi". Ta ɗan yi shiru kafin ta ce"Ai idan aka raba gidan zan dai samu sassauci, na daina ganin yaron nan, baƙinciki zai ragu, in sha Allah yaran nan ba za su yi albarka, sai dai a samu taron yuyuyu, duk shekarun da muka yi tare me ya nema ya rasa da zai ƙwallafawa ransa sai ya haihu?" Ta jinkirta ta ce"A'a Asabe, ba zan iya bin bokaye ba, amma fa da kissa da makirci sai na ga bayanta a gidan nan, sai ta tafi ta bar min yaran da take ɗaga kai saboda su, kuma na yi yadda na so da su, na yi musu kisan mummuƙe, shi ma Isma'il ɗin ai munafuki ne, ba ki ga yadda yake sonta ba". Ta yi shiru na ɗan lokaci kafin ta ce"Ai kuma ba zai yiwu ba, ko sakar min fuska ba ta yi, ba na tunanin zan samu hanyar da zan saka mata magani a lemo har ta sha". Ta ce"To shikenan, ma yi maganar". Daga haka ta gama wayar, na kalle shi ba ga yadda yake ta huci alamar ran shi ya ɓaci sosai, na juya na koma ɗakina, shi kuma ya shiga nata ɗakin. Tana shirin zama a kujera ya shiga, ta ƙaraso tana "Sannunku da zuwa ranku ya daɗe". Za ta rungume shi ya zame ya zauna. Ta sha jinin jikinta ta zauna ta ce"Ranku ya daɗe me ya faru? Wane ne ya taɓa min ku? Allah Ya huci zuciyarku". Ya ɗaga mata hannu ya ce"Malama ki dakata da wannan pretending ɗin haka, zai fi kyau ki kira ni da Isma'il ɗina, wanda ma kike yi wa kallon munafuki wace gulmar ce za ki dinga ɗora min sarautar banza da wofi?" Sai gabanta ya faɗi, ta ce"Ban gane me kuke nufi ba mai martaba". Ya ce"Kar ki sake ki sake ce min mai martaba daga yau! Na ji komai na san wace ce ke yanzu, na ji abin da yake ranki, na san irin kallon da kike yi min, da kuma mugun fatanki a kan matata da yarana". Zuwa yanzu ta gane tabbas ya ji wayar da ta gama yi ne, don haka hankalinta ya tashi, ya sakko daga kujerar ta durƙusa a gabansa ta ce"Mai martaba ban fa gane ba, ba ni da wani fata a kanku ku fa yaranku sai na alkhairi, yaranku nawa ne, ko wani tuggun matarku ta haɗa mana?" A tsawace ya ce"Idan kika sake yi min jam'u ban yafe miki ba, munafukin Isma'il ɗin ne abun yi wa jam'u da sunan girmamawa? Na ji duk wayar da kika yi yanzu, kina da sauran musu?" Sai ta fashe da kuka ta ce"Don Allah ka yi haƙuri ka gafarce ni, wallahi sharrin shaiɗan ne, da wata ƙawata nake waya, kuma ina faɗa ne kawai ba wai haka ne a zuciyata ba". Ya yi danne-danne a waya ya kunna mata recording ɗin nan, ta gama saurara jikinta har rawa yake yi, ta ce"Don Allah ku yi haƙuri". Ya ce"Lokacin da na samu recording ɗin nan na yi miki uzuri ban ce miki komai ba, amma yanzu tun da har ƙiyayyar taki ta tsallake kan kishiyarki ta hau kan yarana dole zan magantu, Halima ba ki yi min adalci ba, ba ki yi min kara ba, duk yadda nake zaune da ke da zuciya ɗaya? Duk halaccin da na yi miki da tarin alfarma ashe a mara adalci kike kallona? Ke kika nuna kina sona, ke kika nace sai da na fara sonki har na aure ki, muna tare wannan larura ta same ki har ta kai ga an cire mahaifar babu halin haihuwa, a tunanina adalcin da zan yi miki shi ne na zauna da ke da kyautatawa da soyayya kamar yadda muke a da, sannan kar na juya miki don na yi aure matar ta haihuwa, iya yina na yi ƙoƙarin yin hakan, amma ke ma a tunanina za ki yi min adalci ai, a zatona da kanki za ki ba ni shawarar na ƙara aure, tun da dai ina da lafiyar da zan haihu kuma ina da halin riƙe wata matar bai kyautu na zauna na ce ba zan yi aure na samu zuri'a ba". Ta ce"Don Allah ka yi haƙuri, na san ban kyauta ba". Ya ce"Ai ba maganar hakuri ba ce, Halima 'yan'una duk irin yadda suke nuna ba sa sonki abun ciwo yake yi min, sun sha zuwa su ce kin yi musu abu kaza, ki saka ni a gaba da kuka ki ce ba ki yi ba, kuma na yarda da ke, idan kin je sabgarsu kullum sai kin ce sun yi miki wani abun, ƙarshe ma saboda ba na so a ci zarafin matata na hana ki shiga jikinsu, na raba alaƙarku, mahaifiyata ce fa Halima? Idan kina da kara da adalci za ki daina zuwa gaishe ta ɗin? Kina kallo za ta yi jinya amma ba za ki je ba, abun fa ba ya yi min daɗi, na yi auren nan kika nuna kin karɓi yarinyar nan hannu biyu-biyu, kike nuna ita ce fitinanniya ba ta so a zauna lafiya, ki ce ta yi miki rashin kunya, ta ci zarafinki ta yi miki gorin haihuwa, ashe duka ƙarya kike yi, burinki kawai ki haɗa ni da matata, to ai kuwa kin ɗauki alhakinta, idan ba ta yafe miki ba sai an yi muku hisabi, ni ma kuma faɗan da kika dinga sakawa ina yi mata ki sani kin ɗauki alhakina, domin ta daɗe tana yi min kallon mara adalci". Cikin kuka ta ce"Ku yi haƙuri don Allah, ku yafe min, na canza in sha Allah ba zan sake irin haka ba, kishinku ne ya ja komai". Ya ce"Haba Halima, ki yi min adalci mana, mene ne ba na yi miki? Kishin kuma har da yarana za ki yi? Ai kuwa duk maso uwa ya so 'ya'yanta, inda da gaske kina sona tsakaninki da Allah ba za ki ƙi ɗana ba, har kina aibata shi da ce masa mai ƙaton kai, sannan wane magani ne ake ba ki shawarar ki zubawa matata? Na mutuwa ne kenan ta tafi ta bar ki sannan su ma yaran a hankali ki ga bayansu ko?" Ta ruɗe ta fara girgiza kai alamar a'a, ta ce"Wallahi ba kashe kowa zan yi ba, na zubar da ciki ne, kuma dama ba yi zan ba, don Allah ki yi haƙuri, na yi nadama". Ya ce"Nadama mara amfani, tun da ba ki yi domin Allah, don haka ban yarda da nadamarki ba". Ta riƙe ƙafar shi tana gursheƙen kuka ta ce"Na san ban yi maka adalci ba, don Allah ka yi haƙuri, ka yanke min hukuncin da zan iya ɗauka, kai ne duniyata ba zan iya rayuwar aure da waninka ba, ban kyauta ba, ka zauna da ni da zuciya ɗaya na sani ka yi min komai, shaiɗan ne ya rinjaye ni, ka yafe ni". Ya ce"Ki shirya gobe za ki je ƙasarku". Ya tashi zai fita, ta riƙe shi gam tana kuka sosai ta ce"Don Allah ka yi haƙuri, ka rufa min asiri, idan ka sake ni ban san wanda zan aura na rayu cikin salama ba, kun uwansa ba za su ɗauki goron haihuwa ba, na san idan shi bai yi min ba danginsa za su yi min ko kishiyoyi". Ya ce"Ai gorin kike nema tun da dai har kike ƙaryar an yi miki, ki shirya dole gobe za ki bar gidan nan, ba sakinki na yi ba, amma ki je na daina ganinki na kwana biyu, duk lokacin da na huce na faɗa miki ki dawo". Bai sake sauraronta ba ya fice daga ɗakin, ya shiga ɓangaren Sayyada, ya shiga ɗakinsa ya kulle, da ta buga masa ma ya ce ta rabu da shi yana buƙatar kaɗaici. Washegari duk magiyar da Hajiya Halima ta dinga yi masa ya ƙi ji ya ce sai ta tafi gida, da ta matsa ya ce to zai sake ta idan har ta ƙara yin musu da shi, a dole ta haƙura ta tafi ɗin. Ni dai ban yi masa maganarta ba, shi ma kuma bai yi min ba, jikinsa a sanyaye yake har kwana biyu, daga nan kuma ya warware muka cigaba da rayuwarmu hankali kwance, duk da laulayin nan haka nake ƙarfafar jikina ina kyautata masa, ina yin duk wani ƙoƙari don ganin na cike masa duk wani gurbin matar shi, saboda kar ma ya ji kewarta, ni duk a zatona sakinta ya yi, kuma har zuciyata ba na so ta dawo gidan, domin yanzu da ba ta nan rayuwar gidan ta fi yi min daɗi, kullum ina da miji a kusa da ni, kullum ya zo ɗakina zai shiga, da ni kaɗai zai yi fira da dai sauransu, lallai kishiya ba ta da daɗi, indai irin Hajiya Halima ce, sai idan ta zama dole ne babu yadda za ka yi. [21/11, 9:14 am] Sadiya Abdulrazak: USTAZ ANGON RUKY A haka rayuwar gidan Ustaz ta cigaba da tafiya, duk yadda ya so ya yi sallar dare idan a ɗakin Rakiya yake ba ta barin shi, yana ji yana gani azumin Litinin da Alhamis ma idan a ɗakinta yake ba zai yiwu ya yi ba, saboda karya masa azumin take yi, idan ya ɗauki azumin, da safe yana bacci sai dai ya ji tana lalubar shi, dole azumin ya karye, idan yana ɗakin Rauda ne yake samun sassauci ya samu bacci, tun da ita awa uku ma ya ishe ta, sai dai da safe ma ta sake nema ko na minti talatin ne wataran ma ba ta nema, amma daren nan dai dole ne kawai sai ya yi, idan kwanan Rakiya ya zo gabansa har faɗuwa yake yi, shi bai ma taɓa ganin irinta ba, idan akwai na gaba da harija a halitta to sai dai a ba ta wannan sunan, da ya tsiri yi mata ƙaryar rashin lafiya sai ta ce ai jikinsa ne yake zazzaɓin ba abun ba, don haka ya yi kwanciyarsa ya bar mata aikin za ta iya, to shi Ustaz dama ba wai buƙatar ce ba ya yi ba, kawai yana so ne ya samu bacci ya ba wa gangar jiki hakkinta, amma ba gajiya ya yi ba, don haka abun ba ya yi wa Rakiya wahala, sai ta zama mijin shi matar, ta haye shi ta yi ta abu ɗaya, yau ma haka ce ta faru, tun ƙarfe takwas take ta abu ɗaya, ya baje a katifa ko motsi ba ta yi, bacci yana fizgar shi amma babu damar yi, ga shi washegari da asuba zai yi sammako saboda za su bar garin, zai yi tafiyar sati ɗaya, sanin da ya yi zai huta sosai a sati ɗayan ne ya sa ya rabu da ita take yin yadda ta so, to amma ya ga abun nata ba mai ƙarewa ba ne, tun da yanzu maganar ƙarfe ɗaya ake yi, a sanyaye ya ce"Ke Rakiya anya kuwa ke mutum ce?" Ta dakata ta ce"Wannan wace irin tambaya ce? Hakkin nawa ne ba za ka ba ni ba ko yaya?" Ya ce"Ai ke kakan hakki ma na ba ki, ko na ce kina karɓa, tun da ke ba kya jira ma a ba ki, yanzu dai ɗaga ni mu yi magana". Ta ce"Ai wallahi sai kiran sallar asuba, tafiyar sati ɗaya fa za ka yi ban da rashin tausayi ta ya za ka ce na bar ka? Ni wallahi da za ka yarda ma da na bika, ko a zauren wani gidan ne zan iya kwana indai za ka ba ni hakkina". Takaici ya kama shi, kamar zai yi kuka ya ce"Rakiya ki ɗaga ni haka tun da dai ba katako kika samu ba, ba kuma babyn roba ba ne ko na'ura". Ta ce"Gaskiya sai dai ka yi haƙuri wallahi, na sati ɗaya na zan nema, kuma wallahi duk tsiya idan ka dawo a ɗakina za ka sauka don ba zan karɓi ragowa ba, ni dama shi yasa fa na ƙi aurenka tun farko, don wannan fashin kwana ɗayan ba ƙaramin cutata yake yi ba". Ustaz ya tattaro ƙarfinsa ya wancakalar da ita, ya tashi da sauri ya sauka daga katifar, sai dai yana tashi tsaye ya zube rigijaa saboda ƙafafuwansa sun sage, ya fara furta "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allahumma ajirni fi musibati wa aklifli khairan min ha". Rakiya ta taho da sauri tan faɗin"Subhanallah! Shi yasa na so ka tsaya mu ƙarasa, mararka har yanzu da nauyinta shi ne dalilin faɗuwar". Ustaz ya ce"Ke Rakiya bari na faɗa miki gaskiya, aurena da ke ba zai yiwu ba, bi ma'ana za ki koma gidanku nan ba da jimawa ba, dalili kuwa shi ne na gano cewa ke ba bil'adama ba ce, don haka ki yi ta kanki na yi ta kaina". Nan take ta gigice ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yi haƙuri Malam Ashiru don Allah ka rufa min asiri, idan ka sake ni ina zan kama? Wallahi tun da nake yin aure ban taɓa ganin jarumi irinka ba, ka yi haƙuri don Allah, na yarda zan rage". Ya ce"A'a wallahi Rakiya ki yi ta kanki na yi ta kaina kawai, tun da dai ni ba na'ura ba ne, ke ba alkhairi ba ce a tare da ni, kin hana ni sallar dare wacce na ta zame min jiki tun da kuruciyata, sai yanzu da ya kamata na ƙara ƙarfafa ibada za ki hana ni? Azumin nan kin hana ni yi, ga Ramadan yana tahowa to ya kike so na yi kenan? A'a Matata Raudatu ni ta ishe ni, gaskiya dole na san abun yi". Ta dinga ba shi haƙuri, ya ce"Ba zan haƙura ba, tun da ke ba ki san zuru ba, awa nawa kika yi kina abu ɗaya? Kin mayar da ni mace ke ce namiji saboda tsabar raini, a wani lusari, ragu kike kallona, ni gaskiya ba zan ɓoye miki ba matuƙar aka cigaba a haka to wataran zan suma kina can kina hidima ba ki sani ba, to ke nan wa gari ya waya idan na mutu?" Ta ce"Ni ya waya, wallahi ni gari ya waya, tun da na shaida ba zan samu kamarka ba, ka yi hakuri Malam, na yi alƙawari zan rage in sha Allah". Ya yi banza da ita ya bar ɗakin, ya tafi ɗakin Rauda ya fara ƙwanƙwasawa, ta kira shi a waya ta tambaye shi shi yake bugawa? Ya ce shi ne, ta zo ta buɗe, yana shigowa ta rungume shi tana cewa"Alhamdulillah, dama na kasa bacci, ina tunanin yanzu ko yaya ne ba zan samu ba a daren nan? Ga shi idan ka tafi sai ka yi sati ɗaya, ashe kai ma hankalinka yana wajena, mu je don Allah ka taimake ni I will miss You". Ustaz ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na guji masifa na tarar da bala'i, to ga ni, ga ni Rauda tunda ke ma kin zama abin da kika zama ki kai ni gadon ki yi min fyaɗe, to ni yanzu ko fyaɗen aka ce za a yi min ma Allah na tuba me za a samu? Babu komai fa waccen jarababbiyar ta ƙarar da ni tass, amma ga ni nan ai, tun da kar ki ga na tauye miki hakki". Ya kunce tazugen shi wandon ya zube a ƙasa. Jikin Rauda ya yi sanyi, sai ta rungume shi ta fara kuka tana faɗin "Ai ga illar ƙara aure nan ka gani, muna zamanmu lafiya muna gamsar da juna amma ka auro wacce ta fi ƙarfinka, ni dai gaskiya ba zan iya ba, kullum haka kake zuwa ɗakina a gajiye, duk wani zumuɗi ka daina yi a kaina, idan ka ga ba za ka iya ba kawai ka sallami ɗaya a cikinmu, dama ai na san ba zai yiwu hariji ya auri harija sannan ni lafiyayyiya na zauna a tsakiyarku ba". Ustaz ya ce"To Rauda ke ɗin ma ina kika ga lafiyar? Au ke yanzu jira kike yi wani ya faɗa miki ke harija ce? Da ba ki zama harija ba Rauda ai ke ma za ki dinga sassautawa kanki, ba wai kodayaushe ki ce kina buƙata ba, gaskiya idan na dawo daga tafiyar nan dole ku zauna mu san abun yi kawai, domin ba za ku hana ni neman halak ba, ni idan aka cigaba da tafiya a haka to wallahi ba zan ɓoye muku ba, za ku iya nema na ku rasa, na tafi can wani yankin na dinga ba da fatawa kawai, da rana na yi azumi da daddare sallah da karatun Qur'ani, ai ba dole ba ne kashe arnan, ke akwai ma arna na amana wanda ko a zamanin da ba a kashe su, to na ga wannan zamanin da arnan ma ake rayuwa, ba zan iya ba kowa ya yi ta kansa a to". Rauda jikinta ya yi sanyi ta ce"Ka yi haƙuri". Ta kai hannu za ta gyara masa wandon, ya matsa yana cewa"Innalillahi wato Rauda duk bayanin nan da na yi miki ta bayan kunne ya wuce?" Ta ce"Ni fa gyara maka zan yi". Ya ce"Ba na so". Ya shiga banɗaki ya yi wanka, ya kwanta bacci ya ɗauke shi, ita ma ta yi baccin tana ji a ranta ko me za a yi ba za ta yarda a raba ta da mijinta ba, don ta ɗanɗana ba ta ji daɗi ba, to ita ma Rakiya a nata ɓangaren haka take rayawa, ita da Ustaz mutu-ka-raba, domin yanzu ta ga mijin zama. [21/11, 11:08 am] Sadiya Abdulrazak: ƘARSHE Da alama dai mai martaba ya yi fushi da Hajiya Halima sosai, domin kuwa sai da ta yi wata biyar a gida, duk magiyar da take yi masa ya ƙi ba ta damar dawowa, da ta gaji da gashin da kanta ta sanarwa iyayenta laifin da ta yi masa, sam ba su goyi bayanta, don haka suka zubawa Isma'il ido ya yanke hukuncin da ya ga dama, ƙarshe Sayyada ta dinga kira tana roƙonta ta yi haƙuri, idan ta faɗa masa ta yafe mata ƙila zai yafe shi ma ya yi mata afuwa, idan Sayyada ta yi masa maganar ko ƙala ba ya cewa, ƙarshe ma sai ya gargaɗe ta a kan kar ta sake yi masa zancenta, ganin haka ya sa ita ma Sayyadar sai ta ga dama take ɗaukar wayar Hajiya Halima idan ta kira ta, idan ba ta so ba sai ta ƙi ɗauka, sai da ya mula ya mulmule sannan ya je ya dawo da ita, a gaban iyayenta ya yi gargaɗin idan ya sake kama ta da irin wannan neman fitinar komai zai iya faruwa, ta ce ta amince, sanda ta dawo cikin Sayyada watansa bakwai, da fari ta so shiga jikin Sayyada a ƙoƙarinta na nuna komai ya wuce yanzu za su zauna lafiya, amma Sayyada ba ta ba ta dama ba, saboda ta tafi a kan duk wanda ya ce ba ya sonka to ba zai taɓa sonka ba sai dai don wata manufa tashi, don haka take taka-tsan-tsan da ita, haka zamansu yake kadaran-kadahan, sai dai idan Abiy da Daddy sun shiga ɓangrenta ba ta hana su, kuma ta bi dangin Ismail duk ta nemi yafiyarsu, ta cigaba da shiga dangin idan sabga ta tashi za ta je a yi komai da ita, su ma kuma sun karɓu nadamarta, yanzu idan Sayyada za ta je gidan duk sati tare suke zuwa, duk da har yanzu ita ɗari-ɗari take yi, amma Hausawa sun ce motsi ya fi laɓewa. Allah Ya sauki Sayyada lafiya, ta haifi 'yarta mace, ta ci sunan mahaifiyar Isma'il ɗin ana ce mata Mimi, a wannan haihuwar Hajiya Halima ta shiga cikin mutane an yi taro da ita, duk da ba a san mene ne a zuciyarta ba. SAYYADA Soyayyar mijina kullum kamar linka min ita ake yi a zuciyata, ji nake kamar na fi kowa dacen miji, muna farantawa juna, ya so ya yakice sarautar shi amma inaa ya riga ya saba, wataran sai ya manta ya dinga yin magana da jam'un nan, ni ma idan na so tsokanar shi ina yi masa, ya biya mana mun je umara mu duka har Hajiya, aka bar yaran a gidanmu, amma mun tafi da Mimi, bayan mun dawo ya yi min alƙawarin idan na yaye Mimi kuma ban samu wani cikin ba ya yi min alƙawarin zan je aikin Hajji, sai dai kash! Kafin na yaye ta na samu wani cikin, nunawa da na yi ban ji daɗi ba kawai sai da muka kusa yin faɗa da shi, ba dama na ce zan yi hutun haihuwa sai ya ce na na son shi, ba na tausayin shi, so nake ya tsufa babu 'ya'ya, ƙarshe har da cewa zai auro wacce ba za ta gaji ba, idan ya ce haka sai na kwana ina fushi, saboda tsananin kishin shi da nake ji, tsoro nake wata ta zo ta raba ni da shi, ban je ba a shekarar, amma ya wanke min zuciyata, tun da ya biyawa iyayena sun je, haihuwa ta uku na haifi ɗa namiji, kuma a ranar ya yi min alƙawarin zan huta, ya cika alƙawin kuma, domin sai da na yaye ɗan, na je aikin hajjin da nake buri na dawo sannan na daina planing ɗin. Yanzu ne na gane yadda ake yin tsantsar soyayya ba irin ta Saddam ba, wataran idan ina tunanin irin abubuwan da na yi a kan Saddam sai haushi ya kama ni, na wuni cikin ƙunci, na dinga tunanin to me ma na gani a jikinsa? Me ya ja hankalina har na aikata haka? Shi yasa kullum addu'a nake yi Allah Ya raba zuri'ataeda sharrin makauniyar soyayya, Allah Ya tsare musu mutuncinsu ba don halina ba. Isma'il ya saka yaran a makaranta mai kyau, sannan da daddare tare muke zama mu koya musu wani karatun, Hajiya Halima ma idan ta so tana zuwa a zauna da ita a falona a yi fira, zaman lafiya dai ya wanzu a gidan Masu martaba. USTAZ Yana dawowa daga tafiyar nan ya zaunar da Rauda da Rakiya suka tattauna, har zuciyarsa ya so ya saki Rakiya, amma da ya sanarwa mahaifiyarsa sai ta fashe da kuka ta ce so yake ya tona mata asiri ya tonawa kansa, tun da ita Rauda idan ta so islancinta haka nan ma za ta iya cewa sai ya sake ta, kuma gidansu babu kwaɓa babu harara, don haka Rakiya ce gatansa, kuma ko bayan ranta ba ta amince ya sake ta ba, ya ba ta haƙuri ya ce ya amince, amma dole ya saita gidansa. Ya yi gyaran murya ya ce"Assalamu alaikum ya ku matana masu albarka". Suka amsa sallamar. Ya ce"To ku saurara ki ji ni da kyau, a gaskiya wannan lamarin na zamanmu akwai gyara a ciki, mu mutane ne, kuma ba don kashe arna Allah Ya halicce mu ba, saboda haka mu yi wa kanmu adalci, mu dinga abun nan saffa-saffa, a yi na Musulunci a haƙura da na kafirci, Allah Ya yi mu mu duka masu yawan buƙata, to Alhamdulillah mun gode masa, amma ke Rakiya ki sani ba fa abinci ba ne, yau ko abinci ai ana ƙoshi, duk jarabata ko sanda na yi auren saurayi bi ma'ana zamanin Maraƙisiyya ban kwana ina kashe arna ba, to don haka ki ajiye wannan ƙudurin naki a gefe, duk dare idan Allah Ya ba ni iko zan dinga biyawa duk wacce nake ɗakinta buƙata daidai gwargwado, bi ma'ana mastaɗa'a, za a yi bacci, sannan za a tashi a yi sallar dare, da asuba za a dinga haɗuwa a falon Rauda ina biya muku karatun Qur'ani da hadisai, da ɗan sanin da Allah Ya ba ni, duk wacce ta ga haka ya yi mata shikenan, wacce ta ji ba ta gamsu ba ta yi bayani ga biro da takarda yanzu na sallame ta". Rauda ta ce"Na amince, Allah Ya sa mu dace". Ya kalli Rakiya ya ce"Ke fa?" A sanyaye ta ce"Shikenan, tun da ya zan yi?" Ya ce"Ai babu dole, idan kina ganin za ki samu wanda ya fi ni ki faɗa a sallame ki". Ta ce"A'a, Allah Ya ba mu zaman lafiya". To daga nan gidan Ustaz ya hau kan saiti, aka daina ƙure kashe arna, kowacce yana ba ta hakkinta iya yadda zai iya, sannan wannan karatun na asuba sai ya kawo fahimtar juna tsakanin Rakiya da Rauda, dalili kuwa shi ne, ita Rauda kanta yana ja, ana yin karatun za ta ɗauke, saɓanin Rakiya da take shan wahala kafin ta iya, kuma Ustaz sai ya kafa musu wani sharaɗi, duk wacce ba ta yi karatun yadda yake ba to ranar kwananta zai zuge tazugensa, wannan kuwa shi ne babban tashin hankalin Rakiya, don haka idan ba ta iya ba sai ta je ta roƙi Rauda ta ƙara koya mata, gudun kar a bar mata arna a raye, da haka har suka saba ake yin fira, suka samu kusan lokaci ɗaya, Rakiya ce ta fara haifo ɗanta namiji, bayan sati biyu Rauda ta haifi mace, Ustaz ya roƙi alfarmar Isma'il kan yana so yaransa su saba da juna, domin yanzu Dawoud ne a gefe, don haka duk sati sai an kawo shi gidan Ustaz wani satin kuma shi Ustaz ɗin sai ya kai yaran nashi gidan Sayyada, ta haka ne Dawoud ya gane wane ne ainahin mahaifinsa. Wannan shi ne ƙarshen yadda gidan Ustaz ya kasance, kuma shi ne ƙarshen labarin na duka. *ABIN LURA* Sunana labarin nan ku yi mana adalci ba ku yi min adalci ba, tun da aka yi jam'u za a fahimci adalcin ba mutum ɗaya ake neman a yi wa ba, da farko Sayyada ce take neman adalci a wajen Saddam, saboda ya lalata mata rayuwa kuma ta sadaukar ne saboda so, amma ƙarshe sai ya bayyana shi ba ma sonta yake yi ba, ba shi da niyyar aurenta. Adalci na biyu kuma iyayen Sayyada ne ba a yi wa ba, saboda sun bawa Sayyada tarbiyya daidai gwargwado amma sai ta yi fatali da wannan ta biyewa saurayi ta ɓata sunan gidansu. Daga baya ta yi nadama, adalci na uku shi ne ya kamata iyayen su yi mata uzuri su yafe mata, amma Baba ya ƙi yafe mata, wanda hakan ne ya sa ta faɗawa halaka a gidan Ustaz har ta kusa rasa rayuwarta. Adalci na huɗu shi ne, a lokacin da Saddam ya so su sasanta da Sayyada lokacin suna tare a kan rikicin hana ta haihuwar nan da ƙara aure da ya yi, Saddam ya yi nadamar azabtar da ita da gaske, ya so su samu maslaha, amma ta ƙi ƙarshe har ta nemi ta nakasa shi, wannan ma ba ta yi masa adalci ba. Sannan Ustaz da ya auri matan da masu irin larurar shi ba wannan ma rashin adalci ne, saboda akwai cutarwa a cikin lamarin, da Allah Ya halicci hariji sai ya halicci mace harija saboda a samu adalci ta kowace fuska. Adalci na gaba kuma Hajiya Halima ce ba ta yi wa Isma'il adalci ba, ya zauna da ita da larurarta, ko bayan ya yi aure ya haihu bai canza mata ba, bai yarda an ci zarafinta ba, amma sai take nuna baƙin ciki ga samun ƙaruwar shi, wannan ba ta yi masa adalci. Da dai sauran abubuwa suna nan idan kun yi nazari za ku gano su. Abin da na rubuta daidai Allah Ya haɗa mu a ladan, kuskuren da na yi Ya yafe min, Tammat bi hamdullah! 08028966015