[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* Daga marubuciyar: Maimoon A'isha Humaira Diyam Tagwaye Jidda And now..... Safiyya *Episode One: Bon appetite!* Breakfast is Served💔 Bismillahir Rahmanir Rahim Ina rokon Allah ya bani ikon rubuta alkhairi, ya hana ni rubuta sharri. Assalamu alaikum dearies ❤️ Fatan munyi azumi da sallah lfy. Allah ya karbi ibadun mu ya sa muna daga cikin yantattun bayin sa Ameen. So, kamar yadda nayi alkawarin rubuta Safiyyah after sallah, gashi nan zanyi kokarin cikawa 😁. Ku dai ku taya ni addu'ar Allah ya bani ikon cikawar. Lol Believe me, dama nayi niyyar yi ne on an impulse, sai daga baya kuma na fara cewa "anya kuwa?" But then na riga na fada muku and duk sanda nayi magana ina matukar kokarin ganin na cika ta, sai dai when it is beyond my control, as nobody is perfect. So, we will try insha Allah, but you will have to be patient with me idan an samu rashin update akan lokaci, ina so ku saka a ranku cewa ina iyakacin kokari na. Kamar yadda na faɗa, littafin Safiyya hopefully zai zo a matsayin free tun daga farkon sa har karshen sa insha Allah, depending on in mun samu sponsors at least twenty, ku kuma readers ina rokon alfarmar ku bada haɗin kai wajen showing support to the sponsors dan suji dadin cigaba da siya muku littafin Safiyya kuna karantawa, idan babu sponsors, littafin Safiyya zai koma paid after the free pages. I hope we will enjoy this journey tare da Safiyya and Gidado, it is going to be rough 😁, but I promise you a smooth landing. *Him*👳🏻 "Tell me you love me" yaji muryar ta ta daki dodon kunnen sa kamar a yanzu ne take yi masa maganar. Ya saka hannayen sa biyu ya toshe kunnuwansa sannan ya rintse idanun sa da karfi amma sai ya zama kamar kara clearing vision and hearing dinsa yayi. Abinda ya manta shine daga cikin kansa muryar take fitowa ba daga surrounding dinsa ba. A idonsa yana ganin fuskarta, as clear as the moon when it is full. A zaune a cikin motarsa, fuskarta dauke da murmushin da ya kasance tamkar maganin dukkan damuwa a gare shi, idanuwan ta cike da soyayyar sa. "Tell me you love me" ta fada tana saita camera din wayar ta a fuskarsa, ya saka hannu daya ya kare fuskarsa yana murmushi. "Stop it!" Ya ce cikin muryar dariya, she giggled sannan ta chanja angle din camera din zuwa inda bai kare ba a fuskarsa. "Ka fada mana to, why are you shying away from a simple question. Do you love me?" Ya bude fuskarsa yana kokarin frowning amma ya kasa, baya iya bata rai in dai yana tare da ita. Ya jingina kansa a headrest din kujerar motar yana kallon camera din tata yace "do you need to ask?" Tace "of cause. I want to hear you say it" ya lumshe ido ya bude yace "what is with the camera then?" Tace "as evidence. I want to record you say it sannan in ajiye as evidence yadda idan nan gaba ka ce baka so na ina da shaidar da zan shigar da karar ka zuwa kotun masoya". Yayi dariya sosai yana kokarin ture camera din tata amma sai ta matsar away from his reaching hands, ta ce "confess! Say you love me" ya ajiye hannunsa ganin bata da niyyar bashi wayar yace "common! Why do I have to say it? Me yasa ke ba zaki fada ba sai ni?" Ta daga gira tace "because I say so... Kuma duk abinda nace ina so shi nake samu. Now I want you to say you love me". Ta karasa cikin turo bakin shagwaba. Yayi ajjiyar zuciya "you are impossible Piya. Me zan fada miki ne wanda baki sani ba?" Tace "that you love me?" Yace "you already know that ai, you just enjoy.... enjoy.....en.." ta karasa masa cikin kwaikwayon muryarsa "you enjoy teasing me " sai kuma ta yi dariya. "You are right, na san dama ba fada zaka yi ba. I only wanted to see that" ta fada tana nuna fuskarsa, ya shafa fuskar kamar mai neman wani abu yace "see what?" Tace "your face is red my dear. You are blushing" ta karasa tana sake wata dariyar. Yayi ajjiyar zuciya "Piya! You are...." "Impossible" ta karasa masa tana sake kwaikwayon sa. Ya harare ta "stop that" ta maimaita "stop that" ya fakaice ta ya zare wayar daga hannun ta sannan ya juya camerar zuwa fuskarta. Tayi saurin rufe fuskarta da hannayen ta biyu tana dariya, yayi zooming screen din yana karewa kyawawan fingers dinta kallo. "wa na kama?" Ya fada cikin tsokana, "now, tell me you love me" ta bude fuskar ta harare shi tare da murguda baki a lokaci daya, yayi murmushi "in dai har da gaske rashin kunyar kike ji da ita ki fada min inji. Say you love me" ya karasa yana rage murya can kasa. Ta fara laluben handle din kofar. "Ni ka bude min kofa. Ni hostel zan shiga" yace "kin isa ma, ai yau sai kin fada. Kuma inyi recording din ki in ajiye, in munyi aure mun haifi yara sai in nuna musu yadda maman su ta mutu a kaina" ta juya ido "wai ma, wa ya gaya maka haka?" Yace "I know...I just know. Tun ranar da kika fara gani na you just couldn't stay away from me, kinga dan farin bafulatani kin rikice, kince in ba ni ba sai rijiya" tayi dariya "ranar da na fara ganin ka, loving you was the last thing on my mind. Bana jin ma nasan menene love ɗin " yace "huh? Shi yasa kika bar seat din ki kika dawo nawa? Admit it Piya, you were attracted to me" ta juya idonta "shi yasa naga tun daga ranar duk inda nayi sai ka bini, bita zai zai" yace "tabbas, and this is just the beginning, duk inda kika je sai na biki. Naji na yarda ni bita zai zai din ne. Kuma nan gaba zan zama 'mijin kafin ta ce'" Ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, tana jin nauyin idanuwansa a kanta, ya sauke wayar tare da yin ajjiyar zuciya yace "Please Piya, I think it is about time ki kaini gurin Daddy, har yanzu baki gama jan ajin ba wai?" Ta dago kai suka haɗa ido "sai ka lallaba ni kuma ka bani cin hanci" ya gyara zama yana shafa aljihunsa sannan yace "whatever you want, just say it, kin san cewa I can give the world to you idan da tawa ce. I can go to the ....to the..." "End of the earth " ta karasa masa, yace "yeah, right, I can go to the end of the earth for you if you want me to" ta danyi murmushi tana kallon hannun ta, da alama hankalin ta ya fara tafiya wani gurin daban kamar yadda ta kanyi a duk lokacin da yayi mata maganar aure, absent mindedly tace "but earth doesn't have an end, it is spherical" yace "I don't care. Kin dai gane me nake nufi ai. I can do anything for you" bata ce komai ba sai ta juya kanta tana kallon waje, yayin da shi kuma ya rage ido yana kallon ta kamar mai tunani sai yace "but how do you do it?" Ta juyo tana kallon sa tace "do what?" Yace "finish my sentences. You always seem to know abinda yake raina tun kafin in fada" ta danyi kyakkyawan murmushin ta idanuwan ta suna reflecting tarin soyayyar sa da take cikin zuciyar ta tace "because I am your soulmate". ****.        ****.      ****.     ****.    **** "I am your soulmate" yaji muryar ta tayi amsa kuwwa a cikin kwakwalwar sa. Kansa yake ji kamar zai tsage gida biyu. Ya saka hannu ya dafe goshin sa amma kuma sai yaji ciwon kamar a tsakiyar kan yake, amma kuma kamar ba ciwo ba, kamar wuta ce ake hurawa a cikin kan nasa da zafin ta yake saka gumi tsiyayowa daga cikin gashin kansa zuwa fuskarsa zuwa sauran jikin sa. Ba ciwon kan ne ya fi damunsa ba, ciwon da zuciyarsa take masa ne yafi addabarsa. Wani irin zafi take yi masa mai kama da ƙaiƙayi , gashi tana lullube a kirjinsa dan haka babu damar sosa ta. Ya saka daya hannun ya dafe zuciyar tare da yin  ajjiyar zuciya da niyyar rage azabar amma sai yaji tamkar kara kaikayin yayi. Dama wannan shine heartbreak din da ake faɗa, wannan azabar shine abinda yan social media suke wasa da shi har suke kiransa breakfast? Amma lallai duk wanda yayi wasa da wannan to bai taba shiga irin wannan yanayin ba ne ba. Bai taba jin yadda ake ji ba, ba'a taba yi masa abinda aka yi masa yanzu ba. She was his life. For years, bai taba hango future dinsa ba tare da ita ba. Bai taba ko da tunanin cewa zata iya rabuwa da shi ba because she lead him on, ta nuna masa soyayyar da bai taba tunanin akwai algus a cikin ta ba. Ya gama shirin komai na auren ta. Ya gama plan din komai. A mind dinsa har yayan da zasu haifa yayi picturing din su da kuma irin soyayya da kulawar da zai basu. Gidan da zasu zauna ya gama shi tuntuni. Ita kawai yake jiya, green light kawai yake jira daga gare ta and then suddenly bayan tayi tafiya ta dawo she came to his office da katon ciki a jikin ta and said "I am married. I have been married for years. I am sorry" And then she said "it was all a misunderstanding. I never thought you love me. You never said you love me da na gaya maka cewa I am married ". "Damn it!" ya fada da karfi tare da mikewa tsaye kamar wanda aka yiwa allura. Sai kuma ya dafa bango sannan ya koma ya zauna, bai san ya akayi ba sai ya samu kansa da murmushi. "Ka zare Muhammad" ya fada wa kansa "ta haukatar da kai. Shi kenan ta ka ta kare. Yanzu ma gashi nan kana magana da kanka" sai kuma ya daki goshinsa da tafin hannunsa "damn you" sai kuma ya sake yin wani murmushin. May be haukan will be a blessing. At least in ya haukace gidan mahaukata za'a kai shi ayi tayi masa alluran bacci har karshen rayuwar sa. Then he wouldn't have to think about her. Then he wouldn't have to miss her, miss her smile and laughter, miss the feeling of blood rushing through his body whenever he gets close to her, miss the feeling of excitement whenever his phone rang and he saw her name "Piya❤️". He already miss tsokanar da take masa, tana enjoying tsokanar sa sosai saboda sunan kakanta ne dashi, she used to say "Malam Muhammadu dan fulani, ka ga yar kyakkyawar budurwa shine ka gudo daga riga ka zo ka makale mata" To ko wannan ma tsokanar ce? Yaji wani irin hope ya ratsa zuciyar sa . Cikin sauri ya fara neman wayarsa har yana zubar da wasu daga cikin takardun kan desk din, ya dauka da sauri yayi dialing number din ta sannan ya saka a speaker, a ransa yana karanto addu'ar da bai ma san addu'ar menene ba. Wayar ta shiga amma har ta gama ringing ba'a dauka ba. Ya kira daya layin nata shima ya gama ya katse bata dauka ba. Sai ya kuma kiran na farkon "The number you are trying to call is not available at the moment....." Ya katse. "Damn it!" Ya sake kira, still the same response. Wani bangaren na zuciyarsa ya fara gaya masa cewa blocking dinsa tayi. "she just blocked you guy" ya fada a fili. "she blocked me" ya maimaita da karyayyar zuciya. Ba wasan bane ba kenan. Ba mafarki bane ba kuma. Da gaske ne. Da gaske ne abinda tazo ta gaya masa yanzu. Abinda ya gani a jikin ta yanzu. But how can that be? How evil can she be? Ta yaya zata kasance mai aure through out all zamantakewar su? Ta yaya zai kasa ganewa? "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" Ya fada a fili. He told her that he hates her amma kuma few minutes later babu abinda yake son gani a duniya sama da ita. Babu abinda yake so sama da ita. Babu kuma abinda yake ƙi sama da ita. Is that even possible? ****.    ****.    ****.    ****.    ****.     *Her* 🧕🏻 Nayi kokarin dora thumb dina a ignition amma sai na kasa saboda yadda hannuna yake rawa. Na rike hannun da daya hannun da niyyar bashi support amma sai suke rawar a tare. Sai na hada su duk biyun na rungume a kirjina tare da jan dogayen numfashi sau uku ta hancina ina saki ta baki na da niyyar calming nerves dina down ko dan na samu damar driving zuwa gida, dan na tabbatar idan nayi driving a halin da nake ciki to kuwa akwai matsala ba karama ba, but part of me didn't care about matsala, a percentage of that part even hoped for matsalar, amma nasan in dai har matsalar da nake fata ta faru bisa ganganci ko son rai na to zan hadu da ubangiji na dan shine ya bani rai kuma shi kadai ne yake da ikon karbar ran nawa. Na sake attempting kunna motar, ta tashi sannan na saka ta a drive na dauki hanyar fita daga school ɗin, a raina ina tabbatar wa da kaina cewa wannan shine ganin da zanyi wa makarantar na karshe kamar yadda na yiwa Muhammad kallon karshe a yau. Absentmindedly na dinga driving ɗin, a hankali kamar mai shiga daki, ba tare da na damu da motocin da suke ta yi min horn a baya na ba, da yawan su in sun gaji da horn din sai su yiwa kansu hanya su zo su wuce ni a guje tare da jeho min kallon banza wanda ko kaɗan bai bata min rai ba. Ni yanzu naci dubu sai ceto. A hanya naga restaurant din da na kawo Muhammad last birthday dinsa, ranar da ta raba mu rabuwa ta har abada. Na tuna maganar da ya gaya min a lokacin. "Wata shekarar ba zata zagayo ba Piya in sha Allah sai da ke a dakina" nayi murmushi cikin yarda da hakan "insha Allah" ya bude ido "da gaske? Da gaske kike kin gama jan ajin?" Na lumshe ido na bude tare da langwabar da kai ina kallon sa "zaren nawa naga yana kokarin tsinkewa. Besides, na ga alamar ba zaka iya rayuwa babu ni ba". Yace "exactly. Ba zan iya rayuwa babu ke ba". Na dauke idona daga kan restaurant din ina kokarin cire tunanin ranar daga raina. In dai har na cigaba da tunanin ranar to ba zan iya karasa wa gida ba, maybe sai dai a karasa da ni. Ina tsayawa a bakin gate, tun kafin inyi horn mai gadi ya bude gate din, nasan dai ya gaishe ni amma banji me yace ba sai kawai na gyada masa kai na shige ciki. Addu'a daya da take raina ita ce Allah yasa kar in hadu da kowa har sai na shiga dakina, bana son ganin kowa a lokacin, bana son kowa ya ganni a halin da nake ciki dan bana son tambaya. Sai dai addu'a ta bata karbu ba, ina yin packing naga Yaya Mustapha shima yayi packing a kusa da ni. Na rufe ido na "ya Salam, not him, not now please God" amma ita ma addu'ar bata karbu ba dan yana fitowa daga motar sa direct window na ya taho, ina kallon sa through tinted glass dina ya tsaya ya gyara zaman hular kansa da kuma collar din rigar sa sannan yayi knocking glass din. Na rufe ido na tare da jingina kaina a jikin kujerar motar, "ya Rabbi" na fada a hankali "ya Rabbi give me strength" sannan na kashe motar na bude kofa da sauri na fita. "Fiyya" ya fada yana kokarin haɗa ido da ni. "Ina kika je haka? Daddy ya tayar da hankalin kowa a gidan nan yana neman ki" sai kuma yayi shiru yana karewa fuska ta kallo "are you okay? Are you crying?" Tambayar da yayi min ce ta saka na shafa fuskata sannan na kalli hannun, ni kaina ban san kukan nake yi ba sai lokacin na fahimci tun daga school nake kuka har gida. Ban ce masa komai ba na zagaye shi na wuce, har na shiga ciki ina jin idanun sa a kaina. "God Please... Allah dan Allah.... Allah kasa ba shi bane ba. I cannot take it idan shine". Sai dana dan tsaya a bakin kofa ina karewa parlor kallo ina lissafin ta inda zan bi yadda ba zan haɗu da kowa ba, duk da cewa ma dai gidan babu mutane sosai dan zuwan mu kenan gari jiya kuma gobe zamu sake barin gari. Kuma babu ma'aikata sosai a gidan tunda ba a garin muke da zama ba. Babu kowa da na gani, dan haka na fara tafiya a hankali making sure ban making sound ba har na kusa hawa stairs, a lokacin ne naji muryar Esther. "Madam? Are you okay?" Na runtse ido na tare da kokarin goge hawayen fuska ta amma ina gogesu wasu suka yi replacing din su. Wannan yasa ban juya na kalle ta ba nace cikin muryar da naji kamar ba tawa ba "I am fine. Don't let anyone enter my room" da haka na cigaba da hawa sama ina jinta tana cigaba da wata maganar da ban fahimci me tace ba. Ina shiga dakina na tura kofa na murda lock sannan na jingina da jikin kofar, a hankali kuma sai na zame na zauna a gurin sannan na dira goshina akan gwuiwowina. Abinda kawai nake bukata kenan tun dazu, seclusion din da zan saki kuka na son raina ba tare da wani yayi min magana ba. A lokacin waya ta tayi kara, da kida na musamman da na saka wa Gidado, kidan da yakan saka zuciyata cikin nishadi a duk lokacin da na jishi saboda dokin jin muryarsa. Na dauko wayar na tsaya ina kallon sunan sa da yake blinking akan screen din "Pyar❤️" Naji wani sabon kukan yazo min "Allah sarki Muhammad" na fada a fili. "Allah ka dubi bawan ka ka bashi sassauci" na tuna da irin bakaken maganganun da ya gaggaya min daxu a office dinsa, amma mintina kadan har hana kira na. It won't be easy for him. It won't be easy for me. Kiran yana katsewa na lalubo block button na danna wa number din sa. Abinda ban taba tunanin zan iya yi ba a rayuwa ta. Amma nasan halinsa a kaina, he won't stop calling hakan kuma yana nufin I might answer, in na amsa kuma komai ya rushe kenan. Sai dai ina dauke hannuna kiran sa yana sake shigowa through my other line. Shima jiran sa nayi ya katse sannan nayi blocking dinsa ta chan din ma. Abinda kawai nake hangowa a idona shine fuskar Gidado a yadda na baro shi a office dinsa da zu. I have never in my life seen someone as broken as he looked. And why won't he? Na yaudare shi iyakacin yaudara, na cutar da shi iyakacin cuta, na kuma tabbatar ba zai taba yafe min ba. Amma a ganina hakan shine dai dai, hakan shine zai fi masa alkhairi, he will heal with time dan ban taba jin wanda yaki warkewa daga heartbreak ba, he will find someone and marry and have children kamar yadda yake da buri, and life will go on while I face my demons alone. Na shafa cikina wanda shine silar komai, a raina ina jin ina ma dai zan iya gayawa Gidado gaskiya, ina ma dai zai iya sanin gaskiyar cikin. Maybe it will reduce his suffering na dan lokaci kadan, but it will torment him for the rest of his life. Ni kuma simplest way out nake nema masa. Karar knocking naji a kofa, banyi magana ba dan nasan muryar ba zata fito ba, aka sake wani tare da magana a lokaci daya, muryar Safina "Fiyya na san kina ciki fa, Daddy ne yake neman ki tun dazu" na girgiza kaina, a raina nace "Daddy, Daddy na" sai kuma na mike da sauri na bude lock ɗin kofar, saurin da na tashi da shi da kuma yanayin da nake ciki ya saka jiri ya debe ni, Safina da take tsaye a bakin kofa tayi ssurin rike ni. "Fiyya? Lafiya kike kuwa? What happened again?" Ban ce komai ba na ture hannunta daga jiki na na kama tafiya da sauri zuwa part ɗin Daddy. Safina ta biyo ni a baya tana cigaba da magana. "Magana fa nake miki Safiyya, at least ki tsaya mana kiji abinda nake ce miki. Ne yake damun ki ne? Nasan kina cikin wani hali and I sympathize with you but that doesn't gives you the right to be rude to us. Dazu naji Yaya Mustapha ma yana gaya wa Mommy cewa yayi miki magana kin share shi. Ko ba komai ai ......" Tana ta maganganun ta ni kuma ina kallon jerin hotunan da akayi wa stairs ɗin Daddy ado da su, hotunan segments na kamfanonin sa, kamfanoni na. A lokacin muka kawo bakin kofar part ɗin Daddy, na juyo da sauri ina kallon ta nace "what exactly do you want Safina?" Ta tsaya tana kallon na cikin mamaki, sannan kuma sai tace "I tried to help you, we, your family, are always trying to help you because we love you. At least a thank you would be....." "Thank you" na ce mata sannan na bude kofar na shiga na mayar na rufe. Ina shiga parlon idona ya shiga cikin nasa, Allah kaɗai yasan irin dadewar da yayi a zaune yana kallon kofa yana jiran shigowa ta. A fuskarsa naga alamun damuwa sosai, ya kalle ni ya kalli cikin jikina. Yanayin fuskarsa kadai ya isa ya saka mai karyayyiyar zuciya fashewa da kuka. Mommy tana zaune a kusa dashi itama tata fuskar cike da damuwa. "Am sorry Daddy" na fada tare da sunkuyar da kaina kasa ina kallon yan yatsun kafata. "You are sorry?" Ya maimaita cikin muryar da take kara nuna halin rashin lafiyar sa. Jirin da bai gama sakina ba ne ya sake ɗibana, na ga ya yunkura da sauri zuwa gurina sai Mommy tayi sauri ta rike shi ta zaunar da shi sannan ita ta taho gurina. Ta rike ni a jikin ta tare da fara faɗa. "Kin gani ai, zaki jawo wa kanki matsala ki jawo wa mahaifinki shima matsala, Safina me kike so ki zama ne ni Sa'adatu?" Sai kuma ta tsaya tana karewa fuska ta kallo. "Me ya faru da ke Safina? Kukan menene kike yi haka ?" Daddy na ga ya sake kokarin mikewa. Nayi sauri na saki Mommy na karasa inda yake na durkusa a gaban sa. Ya koma ya zauna yana kallon fuskata wadda duk da ban kalli mirror ba na san ta kumbura saboda nauyin da naji ta yi min. Ya sauke ajjiyar zuciya. "What am I going to do with you Safiyya?" na sunkuyar da kaina kasa. "Me zan yi miki ne wai?" Ya sake tambayar no one in particular. Ban amsa ba dan bani ya tambaya ba. Ko ni ya tambaya din ma bani da amsar da zan bashi. Mommy ta dawo ta zauna a kusa da shi. Sai naga ya juya yana kallon side ɗin sa, ni ma na juya na taya shi ganin abinda yake kallo Hoton ta ne, tayi kyau sosai tana murmushi kamar za'a ce Safiyya ta amsa. Sai naji ina jin haushinta dan ita ce silar komai. Daddy might not know it yet but ni na sani in my bones and soul cewa ita ce silar komai. Sai dai bani da wani evidence da zan nuna masa. Bani da yadda zanyi in kare kaina. ****.    ****.    ****.    ****.     ****.     **** Please vote, comment and share as widely as possible. Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you…. Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on Whatsaap, Facebook, Intagram and Wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma link na social media account din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my Whatsaap, Facebook and Intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. Yes, we will give this a trial muga yadda zai kasance. After the 10 free pages, we will start posting as soon as we get at least 20 sponsors. Insha Allah this will be a win-win for all of us. And it will be a beginning of a beautiful journey. But if it didn’t work, though it will sadden me but Safiyya will become a “paid” novel. I will announce kudinsa in hakan ta kasance. So ku tayani addua cewa it will work. Lol. Cos I want all my fans to meet the amazing “Piya” and her soulmate, “Gidado” as they embark on their journey of a lifetime filled with so much love and obstacles set by their enemies, or should we call them their lovers? Please share as widely as possible.  For sponsorship, contact 0704 203 0419 on WhatsApp or send a dm to my Instagram page https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ== Save my business number 0704 203 0419 and say hi on WhatsApp dan inyi saving naku. Please, dan Allah, abeg, ban da kira. Sai na jiku, sai kun jini. One Love [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* Daga marubuciyar: Maimoon A'isha Humaira Diyam Tagwaye Jidda And now..... Safiyya *Episode Two: The Young Passengers* Na sauke idona daga kallon hoton zuwa kasa, ita ta jawo min duk abinda yake faruwa da rayuwata na sani, amma kuma na san cewa dan Adam baya taba wuce kaddarar sa, rayuwar da tayi ita ce tata kaddarar, nima kuma halin da nake ciki shine tawa kaddarar, kuma na sani cewa addu'a tana chanja kaddara dan haka har yanzu ban gaji ba kuma ba zan taba gajiya ba wajan gyara rayuwata. She was my role model, she has always been. Courage da determination dinta su suke hana ni giving up a lokuta da dama. Yadda ta chanja rayuwar ta from worst to best haka nima nake fatan chanjawa. Giving up has never been in her dictionary and it is not in mine. Kamar yadda Daddy yake yawan yin comment a lokuta da dama, lokutan da muke good time da shi, cewa her fire is burning in me, cewa I have her zeal, strength, bravery and stubbornness, wannan shi nake so in yi proving right. Maganar Daddy ce ta dawo dani daga tunani na. "Safiyya, daga ina kike? gurin sa kika je ko?" Na dago kai na kalle shi, sai na yi sauri na sake sunkuyar da kaina dan ba zan iya cigaba da hada ido da shi ba. Mommy tace "baban Mustapha, kasan dai ɓata lokacin ka da ranka zaka yi a gurin tambayar Safiyya a game da maganar nan, ba zata yi magana ba, wata nawa ana fama? Wacce irin tambaya ce bamu yi mata ba?" Yayi ajjiyar zuciya cike da damuwa yace "na sani Sa'adatu, na kasa hakura ne, gani nake kamar watarana zata tausaya min a matsayi na na mahaifin ta" Naji hawaye na yana sauka akan hannayena da suke kan cinyata. "Am sorry Daddy " na fada a hankali "Sorry she said" ya maimaita. "Abinda ta iya fada kenan in anyi mata magana tace sorry" ya fada cikin kokarin daga murya, sai kuma yayi shiru yana mai da numfashi. Mommy tace "abinda yasa kika dage da nacin sai mun biyo ta Abuja kenan ko? Kika yaudare mu mukayi tunanin you are after your father's health ashe ke kina da plan din ki da kika shirya ko Fiyya?" Na girgiza kai da sauri amma kuma part of me knows gaskiya take faɗa, except maganar daddy's health, tabbas dan in ganshi na nace sai mun tashi ta Abuja. "Ba kuma zaki fadi ko waye shi ba ko?" Ta sake tambaya with hopelessness in her voice. Daddy yace "ba zata fada ba kin sani. Wallahi da na san zaki iya risking mutuncin ki da na family dinki ki fita ki tafi gurin sa da na ɗana miki tarko, da na saka an biki a baya an gano min ko waye shi, kuma wallahi da nayi masa abinda har ya mutu ba zai manta ba kamar yadda yayi min abinda har in mutu ba zan manta ba, da na rusa rayuwar sa kamar yadda ya rusa taki, da na....." Sai yayi shiru yana jan numfashi a kokarin daidaita numfashin sa da ya fara fita sama sama. Na fara tracing tun sanda na fita har zuwa sanda na dawo a raina, ina so inga ko na haɗu da wani da ya san ni ko kuma na bar wani hint da zai taimaka wa Daddy yayi tracing Gidado, har sai da na tabbatar babu sannan naji hankali na ya fara kwanciya. Ba damuwa ta abinda Daddy zai wa Gidado in ya kama shi ba, cos I doubt idan zai iya yi masa komai, damuwa ta shine in akayi tracing Gidado to zai san komai, zai san gaskiyar komai and his parents will be involved too, our school management will also be involved, wannan duk yana nufin bacin sunan Gidado, sannan yana nufin goga masa baƙin fenti na har adaba. Wannan kuma shine abinda nake gudu, shine abinda zuciya ta ba zata iya dauka ba. Ina cikin tunani na naji Daddy yana waya, "Mustapha kazo sama yanzu ina neman ka". Sai hankali na ya dawo jikina, wancan tashin hankalin ya marsa ya bawa wani sabon tashin hankalin gurin zama a cikin zuciya ta. "God, not him please" na fada a hankali ina mummurza yan yatsun hannuna cikin tsananin damuwa. Tabbas ni nace da Daddy na amince da duk wani hukunci da zai yanke a kaina duk a kokari na ganin na rage masa radadin abinda yake tunanin nayi masa, amma kuma zuciya ta tana kakkaryewa a duk lokacin da ta hasaso hukuncin nasa, na san aure zai yi min, kuma na amince da auren amma kuma damuwa ta shine wa za'a aura min? Wanene Daddy zai zaba min a matsayin abokin rayuwata ta har abada. Shin zai zama blessing to me or a curse? A raina nasan few choices ɗin da Daddy zai iya yi. A kokarin sa na kare mutuncina dana family din mu dole na san auren gida zai yi min. Wannan yayi limiting choices dinsa zuwa mutum uku kacal, mutum ukun da dukkan su babu wanda ba zai iya lasar tafin kafata ba in dai za'a aura masa ni, mutum ukun da duk kan su babu mai sona, mutum ukun da duk kan su babu wanda nake so. Mutum ukun da daya daga cikin su yake da hannu wajan bata tsakanina da Daddy, daya kuma yake da hannu dumu-dumu a cikin halin da nake ciki a yanzu. Sai dai bani da tabbas ɗin who is who. Ba kuma ni da shaidar nuna wa Daddy. But the fork is my only way out..... If only I can find the fork..... If only I can find it's marks.... Muryar yaya Mustapha ta katse min tunani na. Na dago kai muka hada ido sai nayi sauri na mayar da kaina kasa ina jin bugun zuciya ta yana ƙaruwa. Ya zauna a kasa nesa da ni kaɗan. "Daddy gani" Daddy yace "kaje motar Safiyya, check the dashboard camera, find out ina taje dazu, if possible, find out da wa ta hadu". Ban daga kai na kalle su ba har ya fita, sai dai yawun baki na gabaki daya ya dauke, numfashi na ya tokare a kirjina. "Why didn't I think of the damn camera?" Na rafa lissafin way out a raina. Tabbas camera ba zata nuna Gidado ba, amma zata nuna makarantar mu da kuma dai dai inda nayi packing wato kofar building din da yake dauke da offices na some staff. And weekend ne. Few staff ne suka shiga a ranar. If police got involved zasu iya gano wadanda suka shiga a ranar and it will take Daddy closer to Muhammad. Mara ta naji ta rike da wani mugun fitsarin tsoro. Hawayen ido na ya kafe. Na zauna zaman jira ina jina kamar akuyar da aka kai mayanka take jiran turn ɗin ta. Bai jima sosai ba ya dawo ya sake zama a inda ya tashi. "Daddy ta kashe camera din kafin ta fita" ya fada yana kallon Daddy. Na dago kai da sauri na kalle shi. Muka haɗa ido sai ya kuma dauke kai fuskarsa expressionless ya cigaba da kallon Daddy. Daddy yayi ajjiyar zuciya "I should have known. She is always too smart for her age, tun tana yarinya she has always been two steps ahead of mates din ta. But still ban dauka zata yi tunanin wannan angle din ba". Mommy tace "ban taba dauka kawaye zasu yiwa mutum rana ba sai akan case ɗin Safiyya. Da ace tana da kawaye na tabbatar zamu samu wani information ko yaya ne daga gare su. Safina kuma tayi iyakacin nata kokarin" Na tuna da kokarin da Mommy take nufin Safina tayi. A raina nace "munafuka ba" tunanin abinda tayi ɗin ya kara min zafi a zuciya ta. But yaya Mustapha, me yake up to da zai yi wa Daddy karya? Akwai wani abun da yake bukata tabbas. "Tashi ki tafi" Daddy yace Na mike still idona a kasa, har na fara tafiya naji Mommy tace "ko parlor ban yarda ki sake fitowa ba sai in zamu bar gidan nan. Kuma wallahi kika fita sai ranki yayi mugun baci". Na ɗan dakata sannan na juyo ina kallon ta nace "to Mommy" a raina nace na riga na gama abinda ya kawo ni abuja ai, na gama da Nigeria ma gabaki dayan ta, bana fatan wani abu ya sake dawo dani kasar nan. Na kai bakin kofa naji Daddy yace "kai Mustapha ka zauna, akwai maganar da zamuyi" na sake dakatawa tare da rintse ido na, sannan ba tare da na juyo ba, na yunkura na bude kofar na fita. Kafin in shiga dakina na haɗu da Esther duk a tsorace. Ta biyo bayana "Madam am sorry, ban san an shiga dakin ki ba. Sai dana ce mata kar ta shiga. Na dakata da tafiyar ina kallon ta ina mamakin yadda ta daga hankalin ta akan karamin abu nace "it is okay Esther, relax, she is my elder sister ni kaina ba zan iya hanata yin abinda take so ba". Na dauka Esther tana yi min maganar knocking da Safina tayi dazu a dakina ne, sai da na bude kofar dakin na shiga sannan na fahimci ba wannan bane ba. Duk an zazzage contents ɗin cikin jaka ta akan gado, da alama wani abun ake nema sai dai ban san menene ba ballantana in san ko an samu ko ba'a samu ba. Naga wayata a yashe a gefe, na dauka naga ta nuna alamar anyi ta trying budeta an kasa. Na zauna a bakin gado ina tsince tarkace na tare da mayar da su cikin jaka. Na bude wayar using face lock ina kallon hoton da na saka a matsayin screen saver dina. Hoton hannun Muhammad Gidado ne, ya dora akan sitiyarin motar sa, da zubunan azurfa guda biyu a yatsunsa, da agogo a wrist ɗin sa. Na tuna sanda na dauki hoton, muna cikin motarsa ne, motar da take holding most of our memories together. ****.      ****.    ****.    ****.    ****.    **** Lokacin yana yi min korafi ne kamar kullum, yayin da ni kuma nake ƙoƙarin mayar da korafin nasa wasa ta hanyar tsoakanar sa. "Abba yana ta yi min maganar komawa gurin sa da aiki" nace "inye, rich kid.... Irin born with a golden spoon din nan ko? Babu ruwan ka da neman aiki sai neman ka ma ake yi ko?" Ya bata rai "you know what I mean kina so ki chanja magana ko? Dazu har fushi yayi, he thought pride ne ya saka nake zaune a makarantar nan bana so inyi aiki a karkashin ss and I am hurt that he thinks that" na gyara zamana with a serious face nace "then do what he wants. You are just enslaving your self here and it is hurting me too" Yace "you think so? Tell me in na bar makarantar nan how am I gonna be seeing you? Safiyya ko gidan ku fa ban sani ba and it has been years muna tare, i know cewa ina barin makarantar nan ko ta kaina ba zaki sake bi ba" Nayi shiru ina kallon sa, yace "what? Ba gaskiya na fada ba?" Nace "kasan me yake damunka?" Yace "insecurity, yes, I am insecure when it comes to you, bani da wani concrete stand and I know anytime zaki iya ajiye ni a side and the thought alone is given me nightmares and...." Nace "you once jokingly asked me me yasa nazo makarantar nan out of all the universities in the world, you jokingly said I followed you here because I cannot live without you, I laughed then amma abinda ban gaya maka ba shine gaskiya ka fada a lokacin, I came here because you mentioned ranar nan da muka hadu cewa kana nan makarantar for the time being. I wanted to be with you. I wanted to see you again. I literally threw a tantrum a gaban Daddy akan lallai nan makarantar nake son zuwa" Na fada ina tuna yadda na kwanta ranar na ringa birgima a gaban Daddy ina kuka shabe shabe da hawaye. Bai ce komai ba ya saki baki yana kallona, na sunkuyar da kaina na cigaba "I was hoping in mun sake haduwa zaka karbi number ta. And maybe say you love me" Yace "Piya? Are you saying that you... " Na saka hannu na biyu na toshe kunnuwana "forget I ever said that. Lala la lala" yayi dariya amma naji relief da excitement a cikin muryar sa sosai, hankalin sa ya kwanta ya samu assurance ɗin da yake so. "Piya, you are impossible. But if that is true then ki kaini gidan ku mana please, at least let then know me yadda zamuyi all these the right way" Na gyada kai "soon insha Allah. Na gaya maka family house din mu yana kano shi yasa ban taba kai ka ba, and Daddy bashi da lafiya yana Pittsburgh ganin likita. In yazo gari I will talk to him and he will tell me what to do. We have nothing to worry about". Yayi ajjiyar zuciya "am sorry Piya, nasan ina ta damun ki kullum, i don't know why zuciya ta ta kasa nutsuwa, ina ta feeling restless kullum. But i promise zan gyara halina" ya fada guiltily. Nayi kokarin chanja topic ɗin ta hanyar daukar hoton hannun sa da ya ke kan stirring "wow! rich kid! Wa ya siya maka sabon agogo? Mommy ko Daddy" na fada cikin tsokana, ya kalli agogon sannan ya kalle ni da sigar harara "ni ne rich kid ɗin? An gaya miki mina ɗan zaman kashe wando ne irin ki? Ma'aikaci ne ni if you don't know" Nace "I don't know nawa suke baka but am sure albashin ka ba zai siya maka wannan agogon ba. So, tell me the truth, I promise ba zan fada wa kowa ba. Mommy ce ta siya maka ko Daddy?" Yayi dariya "ask those who call their parents mommy and Daddy that question, misali you. Ni dan gidan Mama da Abba ne. And I don't throw tantrums idan ina son abu" na dafe kai na "shi kenan kuma na shiga uku a hannun ka. Kayi ta tsokana ta kenan har illa masha Allah " yace "tabbas, har ƴaƴan mu sai na bawa labarin yadda kika makale min kike bina duk inda na tafi" na rike bakina ina jin haushin fada masan da nayi nace "me and my big mouth" yace "you and your cute lips". ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    **** Karar knocking kofa ta dawo dani daga tunani na. Ba tare da na dauke ido na daga kan hoton ba nace "come in". Naji an bude kofa an shigo an mayar an rufe, a tunani na Safina ce, sai dai kamshin turaren da naji ya saka na dago kaina na kalli wanda ya shigo. Yaya Mustapha. Kallo daya nayi masa na sake mayar da kaina na cigaba da aikin kallon hoton da yake kan screen din wayata. Ya zauna akan side drawer yana kallo na. Ganin bani da niyyar yi masa magana sai yayi gyaran murya yace "babu godiya ma ko?" Still ban ce komai ba kuma ban kalle shi ba. Yayi ajjiyar zuciya sannan ya mike tsaye ya tsaya a gaba na. "I just saved you and your precious love a gurin Daddy amma ko godiya ba zaki yi min ba?" Na dago kai da sauri ina jin zuciya ta tana yin zafi nace "yaya Mustapha, what do you want? Me kake bukata daga gare ni?" Ya koma ya zauna muna kallon juna yace "at least a little concern. Fiyya ni yayan ki ne and I love you with all my heart amma I can't help but feel like kin tsane ni kuma ni har ga Allah ban san me nayi miki ba. Tunda abin nan ya faru babu abinda nake yi sai kokarin ganin na faranta miki na rage miki radadin abinda yake damun ki. Only God knows how many times nayi wa iyayen mu karya dan in kare ki. I have nothing to do with abinda kika yi, I have nothing to do with decision ɗin iyayen mu na haɗa mu aure. But why are you cold toward me bayan da ba haka kike min ba?" Na dauke idona daga kansa ina maimaita abinda yace a raina, decision ɗin iyayen mu na haɗa mu aure, so shine kenan, shi Daddy ya zaba, and he is the worst among the three. A hankali nace "Dan Allah.... Ka tashi ka fita..." Ya sake yin ajjiyar zuciya yace "okay zan fita. But just know that in akwai wani abu da kike bukata, just let me know " Bance komai ba har ya mike tsaye. Ban ankara ba kawai sai ji nayi ya kwace wayar hannuna. Na mike tsaye da sauri kamar wadda aka dorawa garwashin wuta a cinya, yayi sauri ya matsa daga kusa dani yana kallon hoton yana murmushi. "Wow. Nice hands...... And that skin...... I bet he is Arab" Ban ce komai ba na tsaya kawai ina kallon sa zuciya ta tana tafasa. Ya cigaba "and he is rich too..... Cos wannan wrist watch din nasa zai sayi kayan jikina kaf har da chanji" Ya dawo yazo ya tsaya a gaba na "I feel for you dear. But it is what it is. Allah yasa haka shi yafi alkhairi". Ya ajiye wayar akan gado kusa da ni sannan ya ce "lecturer ne ko student? Ko kuma non-academics ne?" Naji kamar in rufe shi da duka amma ko motsi ban yi ba. Ganin bani da niyyar ce masa komai sai ya daga kafada yace "okay. Whenever you want to talk I will be glad to listen" Daga haka ya juya ya fita. Na koma na zauna na dauki wayata na fara aikin goge ta kamar wadda aka shafa wa datti. "Munafuki" na fada a fili "munafukai. Bunch of munafukai. Dukkan ku munafukai ne" Na tuna tambayar da yayi min akan dalilin da yasa na tsane shi. Tabbas a yanzu kusan na tsani kowa amma tashi tsanar ta musamman ce. Wannan kuma yana da nasaba da sunan shi. Sunan shi aka ambata a lokacin da aka kira ni. Kiran da ya chanja dukkan rayuwar. "Fiyya! Kina ina? Mustapha ne. Jikin Daddy ya tashi mun tafi dashi asibiti. Hurry up" Na rufe idona ina jin maganar tana amsa kuwwa a cikin kaina. And it sounded just like him. "Allah ya isa" na fada a fili. *Him 👳🏻* Ya dauki hours a cikin office dinsa dan har sai da yaga magrib ta gabato sannan ya fita, shima kuma ya fita ɗin ne kawai dan yasan rashin zuwa gidan sa zai tayar da hankalin mahaifansa. A gidan su suna da wata doka da ya fahimci cewa ta samo asali ne tun daga kakannin sa na wajen uba, dokar kuwa itace kowa must be home before magrib komai girman ka in dai kana gari, dole tare zakuyi sallah magrib da Abba, tare kuma zakuyi dinner. A dinner din ne ake discussing must of the issues da suka shafi family. A dinner din ne kuma must of the times ake matsa masa da zancen aure. Ya dinner ɗin jiya ne yayi musu alkawarin yau Safiyya zata shigo gari, and yau din ne yake saka ran zata bashi go ahead na zuwa gurin iyayen ta. Ya rufe office din ya sauko daga stairs din blindly ya bude motar sa ya shiga. Kafin ya tayar da motar ya dauko wayarsa for like the hundredth time ya kira layin ta. Still baya shiga. Ya kuma san ba zai shiga din ba tunda ya tabbatar tayi blocking dinsa. Amma kuma ya kasa daina kiran ta. He just couldn't let her go. Ba zai iya ba. Ya tabbatar ba zai iya ba. Ya san cewa dating dinta da yayi a matsayin ta na matar aure ba laifin sa bane ba tunda bai sani ba, Allah kuma ba zai kama shi da laifi ba, amma kuma in ya cigaba da bibiyarta a yanzu bayan yasan tana da aure to tabbas Allah zai kama shi. Amma ya zaiyi? "I just want to confirm" ya fada a fili kamar mai kokarin kare kan sa. But confirm what? Wanne confirmation yake bukata bayan wanda ya gani a jikinta? Ciki ne fa da ita, cikin ma kuma ya kwana biyu, duk da shi ba mace bane ba amma yasan cikin zai kai around five to six months. Ciki a jikin Piyan sa. Ya rufe ido tare da dora kansa a jikin stirring yana jujjuyawa. Me zai yi ne? Ta ina zai rarrashi kansa? Wacce amsar zai bawa Mama a yau in ta tambaye shi game da maganar da suka yi jiya? Shi dai ba zai ce mata ashe Safiyya tana da aure ba, he can only imagine irin kallon da zata yi masa idan ya fada mata haka. Ta ina zai fara..... Ina zai samu ruwan da zai kashe gobarar da ta tashi a cikin kirjin sa? His worst nightmare have come to be. Safiyya ta barshi.... Bari na har abada. Ya daga kansa ya jingina shi a jikin kujera, komai ma baya yi masa dadi. A lokacin ne yaji danshi a fuskar sa, ya saka hannu a hankali ya shafa sannan ya tsaya yana kallon abinda ya shafo. Hawaye. Sai ya samu kansa da yin murmushin takaici. Kuka? Wai shine yake yin kuka? Ba zai iya tuna sanda yayi kuka ba tunda yake a rayuwar sa. He has always been strong, emotionally and physically. Mama tayi training dinsa to be a strong man. Amma kuma dama can when it comes to Safiyya to he is the weakest man alive, a hopeless romantic. Da ace labari za'a bashi cewa zai yi wa budurwa kuka da tabbas sai ya kusa faduwa saboda dariya. Amma kuma dama hausawa sunce duk abinda kace ba zaka iya ba to bai kama ka bane ba. Ya bude kofar motar ya dauko ruwa ya wanke fuskarsa, there is no way da zai bada damar a gane cewa yayi kuka, ballantana a gidan su, no way. Yana zuwa gida ya tarar har Abba ya fito zai tafi masallaci, Haidar yana take masa baya. Yayi sauri yayi packing a waje ya bisu a baya yana gode Allah daya kasance Abban sauri yake yi yasan da sai ya sha tambaya. Har suka yi sallah suka fito suka dawo gida bai yanke hukuncin amsar da zai bawa Mama ba. A parlor suka zauna kamar kullum suka kamo tashar labarai, ya wayan ce yana ta danna waya dan baya son yin magana da kowa, gani yake in yayi magana za'a gane me ya faru a cikin voice din sa. Sai dai ba abinda yake ganewa a wayar da yake danna wa dan hankalin sa sam baya tare da shi. Dariya yaji an kwashe da ita a parlon, ya dago kan sa sai yaga duk shi suke kallo suna dariya. "What?" Yace yana rarraba ido cikin tsoron kar dai maganar da yake yi a zuciyarsa ce ta fito fili. "Tunanin me kake yi ne haka?" Abba ya tambaya da dariya a muryar sa. "Tunanin Safiyya" Haidar ya fada shima cikin dariya. Amma maimakon Gidado ya taya su dariyar sai ya mayar da kansa ya sunkuyar ya cigaba da danna kira a layin Safiyya. Mama da ta gama guiding Hanifa ta zauna a kujera tana kallon Gidado, fuskarta cike da damuwa. " Me ya faru?" Ta tambaya tana kallon shi. Ya ajiye wayar tare da yin ajjiyar zuciya yace "babu komai Mama. I am just exhausted ne kawai. Tun safe nake aikin marking script har yanzu kuma ban gama ba". Ta gyara zamanta tace "abinda nake gani a fuskar ka ba stress bane ba, damuwa ce, in ma da akwai aiki to akwai wani abun daban. Me ya faru?" Ya mike tsaye yana kirkiro murmushin da ko lips dinsa bai wadatar ba yace "da gaske nake Mama. Bani da damuwa. Ko kadan. Yunwa dai nake ji" ya wuce su ya tafi dining ya zauna a kokarin sa na ganin ya gujewa cigaba da yi masa tambayoyi. Bai jima da zama ba suma suka taho. Yayi saurin wayancewa da zuba wa kansa abinci. Yana jin Daddy da Haidar suna maganganu akan karatun Haidar ɗin, Mufida tana saka musu baki kaɗan kaɗan, yana kuma jin idanun Mama a kansa. Ya debi loma ya saka a bakinsa, ji yayi gabaki daya bakin ya gauraye da daci kamar da ruwan madaci aka dafa abincin, makogwaron sa ya toshe abincin ya kasa wucewa ciki. Haka yayi ta taunawa dan babu damar ya zubar da shi, har daga karshe ya samu ya hadiye shi da kyar. Ya dago kai suka haɗa ido da Abba da Mama a lokaci daya, yayi sauri ya sake mayar da kansa kasa ya cigaba da juya abincin. Abba ya yi magana "Malam Muhammadu, what is it?" Ya ajiye chokalin hannunsa tare da yin kokarin bada uzurin da zai masking damuwar sa "uhmm.... Abba dama ..... Dama maganar aikin da muka yi da kai, ina ganin in ka yarda zan bar wannan din in dawo gurin ka kawai. Wannan ɗin is exhausting. Na gaji". Abba ya sake cewa "shi kenan?" Gidado ya gyada kansa kawai bai ce komai ba. Kamar daga sama yaji Mama tace "ya maganar Safiyyan? Tazo ɗin? Kunyi maganar?" Gidado ya sake daukan chokali ya cigaba da juya abinci ba tare da ya kalle ta ba yace "bata zo ba Mama. Bata samu damar zuwa ba" tace "but am sure kunyi magana da ita a waya ko? Kasan dai next week za'a zo saka ranar Mufida, ka kuma san na jima ina fadar cewa tare zan haɗa ku" ya gyada kai "na sani Mama. Bamu yi waya ba. Zamuyi amma". Sai kuma ya mike. "Bana jin dadi, bana jin cin abincin nan. Zan je in dan kwanta" Mufida ce tace "Allah yasa dai ba zazzaɓi zaka yi ba Hamma, fuskar ka tayi pale. Ya danyi mata murmushi yace "Ameen dear". Daga haka ya nufi hanyar da zata kai shi inda dakunan su suke. Har ya shiga ya rufo kofa yana jin idanuwan iyayensa a kansa. Yana shiga dakin sa direct gaban dresser ya tafi, ya tsaya a gaban full mirror dinsa yana kare wa kansa kallo. Ya saka hannu ya shafa fuskarsa yaji ta dauki zafi kamar mai zazzaɓi. Sai kuma ya lura da abinda Mufida tace fuskarsa tayi fari tas kamar takarda. Sai yaji muryar Safiyya a kunnen sa yadda take tsokanar sa. "Da wata farar fuskar ka anan" Tana fada ne a matsayin tsokana duk he knows she is saying it as a compliment, or so he thought. Duk sanda ta fadi haka shi kuma yakan mayar mata da cewa "da wata beautiful face dinki anan". Ya tuna ranar da ta fara ce masa me farar fuska. Ranar da ya fara ganinta a duniya. Shekaru da dama da suka wuce. Shekaru goma da suka wuce. He was just seventeen years old. And she was eleven years old. ****.    ****.    ****.    ****.    ****.     **** A cikin jirgi ne, ranar da zai bar Nigeria zuwa Manchester , United Kingdom dan fara karatun degree dinsa na farko. An riga an gama yi masa komai dan haka shi kadai aka saka a jirgi ya tafi. Wannan shine karonsa na farko na yin tafiya mai wannan tsahon shi kadai. Tun yana dan karamin yaro, ya kasance yana da aerophobia ma'ana fear of flying, duk sanda ya hau jirgi ya kan ji tsoro musamman a gurin tashi da sauka ko kuma in aka shiga turbulence. A duk sanda zasu yi tafiya tare da family yakan rike hannun Abba ko Mama, har sai jirgin ya daidaita sannan ya saki. A ranar kuma kasancewar babu Abba babu kuma Mama sannan babu kowa a seat din kusa da shi, sai ya kama handle din seat ɗin ya kankame tare da rintse idonsa. Sai dai duk da haka jiri yake ji, kansa juyawa ya ke yi. A cikin haka ne yaji an rike hannunsa. Ba tare da ya kalli waye ba sai ya damke hannun daya rike nasa ɗin da karfi har sai da jirgin nasu ya dai daita. Ya sauke ajjiyar zuciya tare da bude idonsa a hankali, sai kuma yayi sauri ya kalli side din da aka rike hannun nasa. Yarinya ya gani yar karama wadda ba zata fi sa'ar Mufida ba. Ta karkata kai side daya tana kallon sa fuskarta dauke da murmushi. Yayi sauri ya saki hannun ta yana yarfar da nasa hannun "You? Who are you? Where are your parents?" Ya karasa maganar yana duddubawa around them. Sai dai bai ga kowa da yayi kama da iyayen ta ba, kusan ma inda suke zaunen basu da yawa. Ya sake dawo da dubansa kanta yace "where are your parents?" Direct tace "my mother is dead. My father is in Manchester yana jirana" ya koma ya zauna sosai "are you telling me ke kadai aka sako a jirgin nan daga wata kasar zuwa wata?" Ta daga kafada tace "there is nothing to it really. Uncle Ahmad ya kawo ni airport ya danka ni a hannun cabin crew, they will take care of me har mu sauka and my Dad will be waiting" ya tsaya kawai yana kallon yadda take zarar magana yace "awwn, rich kids, yayan Daddy da Mommy. Now if you don't mind i need to sleep. Ki koma wherever it is that you came from. I don't want any trouble". Ta gyara zama. "i won't trouble you. I prefer sitting here" ya bata rai irin yadda yake yiwa Mufida "ke! Bar gurin nan nace miki" amma maimakon tabi umarnin sa kamar yadda Mufida take yi sai ta kyalkyale da dariya tare da kwaikwayon yadda yayi maganar "ke! Bar gurin nan nace miki" ta sake wata dariyar sannan tace "fillo". Yaji wani takaici ya kama shi kamar ya rufe ta da duka, amma maimakon haka sai ya mike tare da ɗaukan headphone dinsa da niyar bar mata gurin. Sai dai yana mikewa jirgin su ya shiga turbulence. Ya koma ya zauna da sauri tare da mayar da seatbelt dinsa, sai da suka fita daga turbulence din sannan ya lura cewa ya kuma rike hannun ta da hannayensa biyu. Ya sake cika ta yana gyara zamansa. Tace "you have aerophobia you cannot help it. There is nothing to be ashamed of" Ya bata rai a ransa yana tunanin wannan wacce irin yarinya Allah ya hada shi da ita yau. Yace "wai ke parents din ki basu warning dinki not to talk to strangers ba?" Ta gyada kai da sauri tace "Mommy did" yace "you just told me mamanki ta rasu" tace "yes, Mommy is my step mom. But she is more like a mother to me because she loves me so much" yace "ohh, shi yasa ba kya jin maganar ta kenan ko?" Ta yi shiru tana kallon sa da alamr bata gane me yake cewa ba. Yace "she told you kar kiyi magana da strangers, amma gashi kina yi min magana ni" ta girgiza kai "saboda you won't harm me" ya bata rai "ya akayi kika san hakan? You don't know me" ta daga kafada tace "I don't know how I know, i just know" yadda tayi maganar yasa yayi murmushi, sannan yace "you are too smart for your own good, zaki iya cigaba da zama anan, amma kar ki dame ni da surutu" ta yarda da hakan, amma kuma bata cika alkawarin ba dan for the hours da suka dauka suna tafiya sam bata barshi ya runtsa ba, labarai dai kam ya sha su, duk yan gidan su babu sunan wanda bai ji ba, Mommy, Daddy, yaya Mustapha, Hassan, Hussain, Safina har zuwa kan yan aikin gidan su. And he held unto her hands sanda jirgin su zai sauka. Sai bayan sunyi landing sannan yace mata "kim fada min sunan kowa a gidan ku amma baki fada min naki ba" tace "Safiyya. Sunana Safiyya Adam Muhammad. Amma yan gidan mu suna ce min Fiyya. I don't know why" "Piya?" Ya maimaita Tayi dariya "Fiyya. With an F and double y" "Piya" ya sake maimaita wa Tayi ajjiyar zuciya "fillo" ya bata rai, tayi dariya. "In kace Piya kana nufin something totally different from my name" ya bata rai yace "me Piya din yake nufi?" Tace "love ko beloved, in India" ya gyada kai yace "ohh" Tace "and ina da wata super power, I can tell you your name. You are Muhammad Auwal Muhammad" yayi sauri ya kalleta da mamaki, sai ta daga masa flight ticket dinsa da ya fadi kasa bai sani ba. Tace "har ka ji tsoro, da wata farar fuskar ka anan". ****.    ****.     ****.    ****     ****.    **** Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you…. Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah. For sponsorship, contact 0704 203 0419 on whatsap or send a dm to my Instagram page https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ== Save my business number 0704 203 0419 and say hi on whatsap dan inyi saving naku. Please, dan Allah, abeg, ban da kira [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* Daga marubuciyar: Maimoon A'isha Humaira Diyam Tagwaye Jidda And now..... Safiyya *Episode Two: The Choices* For sponsorship, contact 0704 203 0419 on whatsap or send a dm to my Instagram page https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ== Save my business number 0704 203 0419 and say hi on whatsap dan inyi saving naku. Please, dan Allah, abeg, ban da kira *Her🧕🏻* Har dare yayi na kwanta bacci babu wanda ya kara shigowa gurina babu kuma wanda ya neme ni sai Mommy da ta shigo ta matsa min  naci abinci sannan nasha prenatal vitamins dina. Tun da na tashi da assuba kuwa nayi wankana na shirya na saka jilbab ɗin da nake fatan zai rage nuna wa mutane cikin da yake jikina. Dama kayana a hade suke ban fito da su daga jaka ba, duk abinda na fito da shi kuma nayi deciding cewa ba zan tafi dashi ba dan bani da karfi na jiki dana zuciya da zan iya yin wani abu akai. Na koma na kwanta a kan gado na nannade jikina da jilbab ɗin, na rufe idona da fatan bacci zai dauke ni ko na samu na ɗan rage ciwon da kaina yake yi min, amma sai dai a maimakon bacci, memories ne suka yi ta overlapping a cikin kaina, memories of yarintata, memories of relationships dina da family dina a da da kuma a yanzu, memories din Gidado and all the hopes we had for a future together, and the memories of daren da ya lalata komai a rayuwa ta, daren last birthday din Gidado. Na tashi zaune tare da dafe kaina da hannayena ina jin yana barazanar tarwatsewa. Sai kuma na daga kaina sama ina kallon hoton da yake facing ɗin gadona, hoton mahaifiyata a kwance akan gadon asibiti rike da yar jaririya a hannunta, fuskarta cike da tsantsar farin ciki. Nayi ajjiyar zuciya, ina ma dai rayuwa tana da control button, ina ma dai zan iya rewinding komai na koma yar jaririya na cigaba da jin dumin mahaifiyata, inama....... Sai nace a fili kamar mai magana da ta cikin hoton. "you set me up to be devoured by the blood thirsty vultures, yanzu gashi sun kassara rayuwata" nayi tsaki na juyawa hoton baya, sai kuma na sake juyawa nace "I miss you though". Knocking din da naji a bakin kofa ya saka na dawo da dubana kan kofar sannan na kalli agogo, 7:35. "Yes?" Nace ina gyara hijab dina tare da sake haɗe fuska. Sai dai kuma ana bude kofar yanayin fuska ta ya juya zuwa murmushi. At last, someone I can talk to, someone who truly loves me. Suka shigo a tare suma fuskokin su dauke da murmushi, na bude musu hannayena amma maimakon su fada jikina kamar kullum sai suka zauna a sides dina sannan suka rungume ni a tare. Nayi ajjiyar zuciya ina kara rungumar su jikina, ina jin yadda suka kara girma duk su biyun, a tsaho yanzu duk sun kere ni. "Yan biyun yaya Fiyya, I am glad you made it. Ina ta jin babu dadi na dauka ba zan ganku ba har mu tafi". Hassan ya dago kansa daga kafada ta yace "kinga gudun da muka yi a mota kuwa? Mommy tace mu hakura mu zauna tunda jiya ma evening paper mukayi amma muka dage sai da muka zo dan mu ganki kafin ki tafi" Hussain yace "Mommy tace zaki jima baki dawo kasar nan ba, haka ne? Amma zamu iya zuwa mu kai miki ziyara in mun gama waec ko?". Na gyada kai nace "duk sanda kuke son ganin mu kuyi min magana ko kuyi wa Daddy magana, za'a siya muku ticket ku tafi. And anything you need, ko menene, ku kira ni ku gaya min". Suka gyada kai a tare, Hassan yace "but this is not fair, Daddy is not being fair to you. Me yasa zai miki aure yanzu? Mommy tace aure zai yi miki da yaya Mustapha. Yaya Mustapha fa for God's sake. It shouldn't be. Kamata yayi a barki kiyi healing, ki kuma samu wanda kike so ku fahimci juna sannan sai kiyi aure"  na kalle shi ina murmushi nace "all that sounds so good. Amma kuma ba haka Daddy ya zaba ba, and I am sure Daddy ba zai zaba min abinda zai cutar da ni ba, da abinda ka fada ɗin shine zai fi min dai dai I am sure Daddy shi zai zaba min, you should be kinder to him". Hussain yace "but what about you. You are obviously not happy" nace "it doesn't matter. Maybe I will be nan gaba. Hussain, a yanzu haka happiness dina kadan ne a cikin irin abinda zan iya sacrificing dan in gyara relationship dina da Daddy, zan iya bayar da komai, ko da kuwa rayuwata ce to have Daddy hug me and say 'I love you Safiyya'" na karasa maganar ina share hawaye da bayan hannuna". Suka yi shiru gabaki daya sannan Hussain yace "he loves you, you know.  Yafi son ki akan kowa" na yi yar karamar dariya mai kama da kuka nace "my dear brother, am not sure about that. To him, I am just a big fat disappointment". Hassan yace "no you are not. He loves you. We all love you". Nayi kokarin chanja topic ta hanyar cewa "sooo, waye yayi driving a cikin ku, naji kunce kun sharara gudu" Hussain yana dariya yace "Hassan ne" Hassan yace "i passed my driving test last week, shine yanzu na gwada skill dina" nace "yayi kyau. Amma a daina gudu da yawa. An kawo muku motocin kenan?" Hassan yace "no... Ta wani friend din mu ne" na bata rai "why? Me yasa ba'a kawo muku ba? Kun sake yiwa Uncle Ahmad maganar?" Hussain yace "munyi masa fa, sai kawai ya rufe mu da fada wai me zamuyi da personal cars bayan akwai motoci a gida" Na fara girgiza kaina ina cewa "nasan akwai motoci a gidan ai, ni nayi niyyar zan siya muku motoci a matsayin gift na jamb da kuka ci. Zanyi masa magana. Allah yasa zai zo yau yayi wa Daddy sallama, zanyi masa magana". Hassan yace "uhm uhm, kar ki sa yayi miki faɗa kema. Yanzu kula da lafiyar ki yafi komai muhimmanci. Ki rabu da shi kawai". Na sake girgiza kai stubbornly "zan yi masa magana". A haka muka cigaba da hirar mu har sai da Esther ta shigo da tray din breakfast ɗina ta kuma sanarwa su Hussain da cewa nasu abincin yana kasa  sannan suka mike suka yi min sallama. Na tashi tsaye nima na rike hannayen su a cikin nawa nace "idan kunje gurin Daddy, be nice to him please, ku fada mishi maganganu masu daɗi and tell him you love him, hug him" suka tsaya kawai suna kallona amma kuma fuskokin su sun nuna cewa sun fahimci abinda nake cewa, a tare suka gyada kai, nayi musu murmushi sannan ta saki hannayen suka fita jiki a sanyaye. Suna fita Mommy ta shigo ta kuma saka ni a gaba sai da na ci abinci, ina ci tana yi min hira. "Gwara ki ci abinci ki koshi dan ba lallai bane ki iya cin abincin jirgi. Kuma gwara ki ci abinci a daki dan ban san waye zai shigo gidan nan yau ba, ko ma'aikatan gidan ma ban yarda su san halin da kike ciki ba, dan hausawa sunce munafukin ka tabarmar ka". Muna nan zaune Safina ta shigo ta zauna tana kallona ina shan tea din da Mommy ta hada min, tace "I will miss you little sister. Though na san ba dadewa zakiyi sosai ba. Kina dawowa kuma sai mu sha biki" ta karasa tana murmushi. Ban ce komai ba har sai da Safina ta mike zata fita sannan na daga kai nace mata "I will miss you too. Allah ya bada sa'ar karatu" tace "Ameen. Nagode" sannan ta fita. Ban fita ba har sai da aka gama saka duk kayan mu a cikin mota, sannan Mommy tazo da kanta tace inje in shiga mota, shima sai data tabbatar jilbab din jikina ya boye cikin sannan ta kama hannuna muka fita tare. Sai dai muna fita compound din gidan motar Uncle Ahmad tana shigowa, driver yana tukawa, Mukhtar a gaba, Uncle Ahmad a baya. Mommy ta tura ni gaba "sauri ki je ki shiga mota gani nan zuwa" amma sai na makale, ina so nayi magana da Uncle Ahmad akan maganar motocin twins. Mommy ta sake turani amma maimakon nayi hanyar motar da zamu tafi airport a cikin ta sai nayi hanyar inda su Uncle Ahmad sukayi packing. Kafin na karasa suka fito, kallo daya Uncle Ahmad yayi min ya dauke kai, yayin da Mukhtar kuma ya taho direct gurinna yana washe baki. Sai a lokacin nayi nadamar kin jin maganar Mommy. Ya tare min hanya yayin da ni kuma nake kokarin wuce shi na tafi gurin Uncle Ahmad. Yace "Fiyya ko gaisuwa babu? Ko nayi wani laifin ne wai? Ni ina ta jin dadin zan samu na ganki ke kuma ko kallo ban ishe ki ba ko?" Na tsaya tare da juyowa ina kallon sa. "Yaya Mukhtar, barka da zuwa, ya hanya. Nice to see you. Bye". Na juya zan tafi ya sake tarar gabana. "Dan Allah Safiyya ki tsaya. You don't have to be cold. Ki bani dama muyi magana ta fahimtar juna please. Minti biyu ya ishe ni" nayi ajjiyar zuciya ina lura da Mommy da ta bata rai a gefe tana kallon mu. Nace "ina jinka" ya gyara tsayuwa sa, na lura da yadda yake kokarin kar ya kalli cikina, yace "ina jin yau kusan shekaru biyu kenan da na fara gaya miki abinda yake zuciya ta. So kin riga kin sani. Ina so ne in gaya miki cewa babu abinda ya chanja a zuciyata a game dake duk da rejecting dina da kikayi the first time. Babu abinda ya chanja a zuciyata duk da wannan abin da kika yi" ya fada yana waving hannunsa around cikinta ba tare da ya kalli cikin ba, naji zuciyata ta tattare ta dawo wuyana, na nade hannuna a kirjina nace "what do you want, Mukhtar?" Ya dago kai yana kallon cikin idona, nima ban dauke nawa ba, yace "you know exactly what I want" nace "no, I don't. Just skip the whole preamble ka gaya min direct. Menene kake bukata daga gare ni". Ya sauke idonsa kasa yana hadiye yawu yace "idan kin amince ..... A matsayi na na dan'uwanki na jini, ina so in kin haihu, zan taimaka miki in aure ki, har abada babu wanda zai san me ya faru. Har abada babu wanda zai san me kika yi" na kankance idona a kansa nace "Mukhtar, a tsakanin ni da kai tabbas akwai wanda yake bukatar taimako, kuma daga ni har kai mun san waye". Na juya da sauri na bar inda yake, raina a matukar bace, blindly nake tafiya ina magana da kaina kasa kasa, ban ankara ba sai gani na nayi a gaban Uncle Ahmad, na dan ja baya sannan na gaishe shi a diririce "uhmm. Uncle. Ina kwana" yana danna wayarsa ya amsa. "Lafiya" har na wuce shi sai kuma na tuna da alkawarin da nayi wa twins dan haka na dawo da baya. "Uncle.....dama ina so zanyi maka magana ne ... Dazu munyi magana da twins akan cars din da nace a siya musu. Shine nace bara in tuna maka maybe ka manta ne". Wani mugun kallo daya watso min ne ya saka a lokaci daya naji ina ma dai jiya da na kwanta bacci yau ban tashi da rai ba. Na ja da baya taku biyu cikin sauri dan a tunani na rufe ni zaiyi da duka amma instead sai yace cikin daga murya "Safiyya? Yanzu rashin kunyar taki har ta kai haka dama? Zamani har ya kai haka lalacewa? Ke sam baki ma damu da wannan abun kunyar da yake jikin ki kike yawo da shi ba har kina da karfin halin tsayawa a gaba na da abun kunya a jikin ki kina bani umarni?" Na juya da sauri na yi gurin motar mu ina jin kafafuwa na suna harhadewa a cikin juna, ina kuma jin idanuwan duk mutanen da suke gurin a kaina. Kafin in kai mota hawaye sun jika fuskata, ta gefen idona na ga twins sun taho gurina amma sai nayi sauri na bude kofar gidan gaba na shiga sannan na rufe da karfi, still ina cigaba da jin muryar Uncle Ahmad yana cigaba da fadar bakaken maganganu a kaina. "Kaf dangin mu ba'a taɓa yin irin wannan abun kunyar ba. Saboda daurin gindi amma wai har tazo ta tsaya a gaba na tana gaya min maganar banza" na saka hannayena duk biyun na toshe kunnuwa na tare da kifa kaina akan dashboard ina cigaba da rusa kuka kamar wadda aka aikowa sakon Daddy ya bar duniya. A cikin kuka na naji shigowar Mommy cikin motar ta zauna a baya tayi min magana amma banji me tace ba, sai dai na dago kaina na fara kokarin goge hawayena. Yaya Mustapha yazo ya bude daya kofar bayan ya taimaka wa Daddy ya zauna sannan ya rufe ya dawo seat din driver ya zauna. Na cigaba da ƙoƙarin tsayar da kuka na dan sam bana son Daddy ya san abinda ya faru ballantana ransa ya baci. Sai dai yaya Mustapha yana tayar da motar naji Mommy tace "ki daina wannan kukan haka tun kafin ki saka wa kanki wata cutar kuma, ki gaya wa Daddyn ku abinda ya faru" nayi shiru ban ce komai ba, sai naji muryar Daddy yace "menene ya faru?" Na sake yin shiru amma kuma sai hawaye na ya dawo sabo. Ya sake magana cikin tsawa "magana nake miki Safiyya, menene ya faru?" Cikin kuka nace "Uncle Ahmad ne yayi min hayaniya a cikin mutane" yayi shiru kamar bai ji ne nace ba, sai kuma yace a hankali "me yace?" Nayi shiru a raina ina jin nauyin maganar. Mommy tace "zagin ta yayi, ya goranta mata akan abinda ya same ta, a gaban duk yaran gidan nan" Daddy ya sake yin shiru, amma duk da ban kalle shi ba nasan ransa yayi matukar baci, ni kuma abinda nake gudu kenan. Har yaya Mustapha ya ja mota sai Daddy yace "tsayar da motar nan Mustapha, zo ka kama ni in fita". Nayi sauri na juyo ina kallon sa hankali na a tashe. "Daddy please" Mommy ma ta rike hannun sa da sauri. "Dan Allah kar ka fita, dan Allah kar ka kula shi. Abinda yake so kenan dama. Mu lafiyar ka tafi mana komai. He isn't worth it. Ko babu komai yanzu mun san inda ya sa gaba". Daddy ya karbe hannun sa da ta rike ya kama handle din kofar yana kokarin budewa. Na juya na kalli yaya Mustapha cikin tashin hankali nace "rufe lock ɗin. Ja motar mu tafi" yayi abinda nace muka bar harabar gidan a guje. Har muka yi nisa babu wanda ya kuma yin magana. Sai daga baya naji Daddy yace "Mustapha kira min Ahmad a wayar ka ka bani shi" na dafe kaina. Ba zai hakura ba dai. Wata irin zuciya ce da Daddy da sam baya barin magana ta wuce sai ya rama. Ina kallo yaya Mustapha ya daukl wayar sa yayi dialing sannan ya saka a kunnen sa, aka dauka sai yace "Uncle Ahmad, Daddy ne yake son magana da kai" sai kuma ya mika wa Mommy wayar ita kuma ta bawa Daddy, ya karba direct yace "kar ka biyo ni airport, bana son rakiyar taka. Allah yayi min komai, bana bukatar komai daga gare ka". Daga haka ya ajiye wayar. Mommy tace "kash. Ni dai ban so ka kula shi ba wallahi" amma a raina sai nayi mamakin abinda yasa naji kamar farin ciki a cikin muryar ta. Bamu jima a airport ba aka kira jirgin mu, na rungume twins da suka biyo mu har airport a baya muka yi sallama, na tabbatar sunyi sallama mai kyau da Daddy sannan nabi bayan yaya Mustapha da yake tura Daddy a wheelchair zuwa cikin jirgi. Sai dana tabbatar Daddy ya zauna comfortably sannan na nemi seat dina na zauna nima tare da sauke ajjiyar zuciya. Bamu dade da zama ba jirgin ya tashi, daga can nesa dani na hango wata ta kankame hannun kujerarta. Nayi murmushi tare lunshe idona ina kallon seat din kusa dani wanda babu kowa a kan sa. Sai kuma na tuno da fuskar sa jiya. How hurt and broken he looked. Na kuma mayar da idona na rufe a fili nace "I am sorry Muhammad. Ina yi maka son da ba zan iya staining white din ka da datti na ba. Allah ya baka ikon cin wannan jarabawar. Allah ya baka wadda ta fini". Sai kuma naji ina jin kishin wadda Muhammad zai samu bayan yayi healing daga abinda nayi masa. Ina kishin rayuwar da zasu yi. Rayuwar da Gidado ya shirya mana zamu yi ni da shi, yanzu dole da wata zaiyi. Dole da wani zanyi. Zuciya ta naji tana tafasa, gashi na kasa cire tunanin daga cikin ta. Na dauko headphone a handbag dina na saka a kunne na na kunna karatun Alkur'ani tare da rufe idona a hankali ina motsa bakina ina bin kira'ar, da fatan zai sanyaya min zuciya ta. Ban san tsahon lokacin da na dauka a haka ba naji an taba ni. Na bude ido naga Mommy a tsaye a gaba na, tayi min murmushi sannan ta taba wuya na tana testing temperature dina. Sai kuma ta zauna a kujerar kusa dani tace "nace Mustapha yazo ku zauna tare ya debe miki kewa yace in ya zauna ma faɗa zakuyi" nayi shiru bance mata komai ba ido na a kasa. Ta cigaba "me yasa kuke rigima ne kullum wai Safiyya? Akwai abinda yake yi miki wanda ba kya so? In akwai ki gaya min ni zanyi miki maganin sa kinji?" Na gyada kai na kawai bance komai ba. Sai tace "ki je gurin Daddy, yace yana son magana da ke". Na mike da sauri tare da cire headphone ɗin kunne na na ajiye, ta rike hannu na "ki bi a hankali kar ki fadi" na sake gyada kai sannan na wuce na tafi inda Daddy yake. Ina zuwa ya dago kai daga karatun magazine din da take hannunsa, ya kalle ni, kallon da ya fi min ciwo akan komai sannan ya mayar da idonsa kan takardun hannunsa yace "seat" na zauna a kujerar da Mommy ta tashi daga kai ina wasa da yatsun hannuna ban ce komai ba. Ya ajiye magazine din yace "kin dai san maganar da nayi miki akan aure ko?" Na gyada kai, yace "baki da baki?" Na amsa da sauri. "na sani Daddy" yace "good. Da nayi niyyar sai dai kawai kiji an daura miki aure, banyi niyyar sanar da ke komai a kai ba. Amma ban san me ya hani ni yin hakan ba. Ban san me yasa nake tausayin ki ba, duk da kuwa cewa ke ba kya tausayi na, ko kadan" bance komai ba, dan ji nake yi duk duniya tayi min kunci. Jin banyi magana ba sai ya cigaba. "Ina tunanin mahaifiyar ki ce. Memory dinta ne yake hunting dina yake hanani aiwatar da duk wani hukunci da nayi niyyar yankewa a kanki. Komai nayi niyyar yi sai inyi tunanin in tana raye zata yarda? Kullum sai nayi tunanin in tana raye wanne hukunci zata dauka akan ki" ya yi ajjiyar zuciya yace "but I guess I will find out soon enough" na dago kai da sauri na kalle shi amma sai yayi sauri ya juya kansa gefe, ya cigaba "babban burina kafin in tafi din shine in ga rayuwar ki ta daidaita, yadda at least ubangiji zai rangwanta min akan  laifin negligence a kula da amanar da ya bani, yadda at least zan samu abinda zan gaya wa mahaifiyar ki idan na haɗu da ita a can". Na goge hawayen kan kuncina a hankali na fadi kalmomin da suka zamar min kamar karatun sallah a cikin watannin nan "Daddy I am sorry". Ya cigaba "wannan dalilin ne yasa nake son yi miki aure as soon as possible. Bana so in tafi ba tare da na yi miki aure ba Safiyya. Bana so in tafi ba tare da rayuwar ki ta daidaita ba. Wannan shine abinda nake tsoro fiye da mutuwar ita kanta" yayi ajjiyar zuciya ya cigaba "nayi magana da likitan da zai cigaba da dubaki a Germany, ya gaya min cewa zasu iya cire cikin idan yayi wata bakwai ba tare da illa ga ke ko babyn ba. Wannan shine abinda za'a yi. Ina so a rabaki da cikin nan ina raye. Sai dai kuma ban san yadda zanyi da babyn ba idan an cire shi. So for the last time ina sake tambayar ki Safiyya, waye uban cikin nan?". Na girgiza kai na da sauri amma na san yin shiru na zai kara bata masa rai, kamar yadda nasan abinda zan fada ɗin shima bata masa ran zaiyi. "Daddy wallahi ban sani ba" na fada cikin rawar murya. Yayi ajjiyar zuciya. "I thought as much. Kamar yadda na fada, ni ina tausayin ki amma ke ba kya tausayi na. Okay let's assume gaskiya kike faɗa. Ba ki san waye ba. Amma ai na tabbatar da cewa kin san waye saurayin nan naki ko? Ko shima ba ki san shi ba" na girgiza kaina sai kuma nace "na san shi Daddy " yace "okay, let's go over the whole story kamar yadda kika bamu. Kince a ranar da abin ya faru you were with him throughout the evening, har dare kuna tare. Haka ne?" Nace "haka ne" ya cigaba "da dare you look him to an eatery. Kuka ci abinci tare daga nan sai aka kira ki, someone claiming to be Mustapha, and that's when it happened. Ko?" A hankali nace "haka ne" yace "okay let me break it down for you maybe ko zaki iya bude idonki beyond soyayyar da kike yi masa ki ga gaskiya. You told him cewa a ranar zan zo gari. Haka ne?" Nayi tunani, tabbas na gaya masa, we were so excited saboda na gaya masa a matsayin another birthday gift da zan bashi, zan kai shi gurin Daddy idan yazo. Nace "haka ne" yace "kuma shi kadai kika gaya wa ko kin gaya wa wani?" Nayi tunani, ni bani da wasu friends da nake wata personal magana da su, na girgiza kai na "ba wanda na gaya wa" Daddy yace "good. And ya san bani da lafiya?" Nan ma na amsa in the affirmative. Ya kuma tambaya "kuma ya san kina da dan'uwa Mustapha, ya san tare zamu taho da shi?" Nayi shiru a raina bana jin dadin direction din da wadannan tambayoyin suke tafiya. Ya katse min tunani na "yes or no" nace "yes, ya sani" yayi murmushi "tambaya ta karshe. Sanda aka kira ki aka yi pretending to be Mustapha, yana zaune a gurin ko ya tashi?" Nayi shiru ban ce komai ba, zuciyata tana bugawa kamar zata bar kirjina. "Answer me!" Ya fada da muryar fada. Na tuno abinda ya faru a lokacin, muna zaune aka kira Gidado a waya, ya dauka baya jin abinda ake cewa sai ya tashi looking for network, and then my phone rang. Na lumshe ido na a hankali nace "baya gurin, ya tafi yin waya" Daddy ya sake yin murmushi yace "and you still think ba shi ya kira ki ba? You still think ba shi bane ba?" Na girgiza kaina "Daddy bashi bane ba" Ya dafe kansa da hannu daya, ina jinsa yana karanto addu'a a hankali, maybe addu'ar Allah ya sanyaya zuciyarsa kar ya rufe ni da duka a cikin jirgi. Ya bude idonsa at last yace min "okay. A cikin biyu akwai daya. It is either duk wannan labarin da kike bayarwa karya kike yi, ko kuma kin san shi ɗin ne and you are doing everything in your power to protect him" na sake girgiza kai stubbornly "bashi bane ba" "Tashi ki bani guri" Daddy ya fada cikin tsawar da nasan mutanen gurin sunji. Na mike da sauri jikina yana rawa, sai kuma yace "A cikin mutum uku ina so ki zabi daya. Ko Mustapha, ko Mukhtar, ko Abdul". Na durkusa a kusa da kafarsa ina kallon yatsun hannuna bance komai ba, tunani na yana rarrabuwa. Farko nayi tunanin already Daddy ya yanke hukuncin aura min Mustapha, tunda har shi kansa Mustapha din ya shigo dakina jiya yana min kurari akan hakan, Safina ma kuma tayi min magana akan hakan in another way, ashe su maganganun su kawai suke yi Daddy bai tsayar da magana ba, ban taba tunanin zai bani zabi ba, ban saka ran zai bani zabi ba, dan haka ban auna choices ɗin nawa ba. Nace "ko Mukhtar ko Abdul, duk wanda zuciyarka tafi amincewa da shi Daddy, ko ba su ba ma kowane ne, anyone but Mustapha. Dan Allah banda Mustapha" "Zauna" yace min yana sake nuna kujerar da na tashi daga kai. Na koma na zauna. Ina ganin yana kokarin daidaita numfashin sa sannan yace "me yasa kika ce banda Mustapha?" Nayi shiru ina wasa da yatsun hannuna. Ba zan iya gaya masa dalili ba, kamar yadda na zan iya gaya masa dalilin da yasa na dage akan ba Gidado bane uban cikina. Akwai wadu abubuwan da ƴa ba zata iya gayawa mahaifin ta ba, mahaifiyarta ta ke bukata, ni kuma bani da ita. Jin nayi shiru ya cigaba. "Mahaifiyarsa tana kaunarki sosai. Ta kuma dora ranta sosai akan auren ku. Asalima dagewarta akan abun yana daga cikin dalilin da yasa na baki zaɓi dan na fara tunanin wani abu daban. Amma kuma Mustapha is like a son to me. No na bashi tarbiyya, kuma yanzu ni nake morar sa fiye da wanda ya haife shi. Shi nafi tunanin zai rike min ke amana akan sauran. Musamman yanzu after what Ahmad did to you". Jin bani da niyyar yin magana ya sake cewa "tashi ki tafi". Na mike na koma gurin da na zauna da farko, na tarar Mommy tayi bacci, na gyara mata kwanciyar ta sannan na zauna na mayar da headphone dina ina lissafa maganganun da muka yi da Daddy. Naji dadin zancen cire wannan kaddararren cikin da yace za'a yi at seven months, meanin6ina da sauran just a month and a half tare da cikin kenan. Na biyu kuma hujjojin da Daddy yake neman kafawa akan Gidado. Daddy was right, kowanne evidence yana pointing directly at Gidado, amma bashi bane ba, na sani in my bones and soul cewa bashi bane ba, amma bani da shaida. How I wish cewa shi ɗin ne ma. It would have made all these easier for everyone. ****.    ****.     ****.    ****     ****.    **** Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you…. Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah. [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* Daga marubuciyar: Maimoon A'isha Humaira Diyam Tagwaye Jidda And now..... Safiyya *Episode Four: The Choices 2* For sponsorship, contact 0704 203 0419 on whatsap or send a dm to my Instagram page https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ== Save my business number 0704 203 0419 and say hi on whatsap dan inyi saving naku. Please, dan Allah, abeg, ban da kira ****. ****. ****. ****. ****. **** Awa 8 da rabi mukayi muna tafiya kafin mu isa garin Berlin, Germany. Daddy ya zaɓi Berlin ne saboda anan ne babban abokinsa Uncle Sufyan yake zaune da iyalinsa. Akwai kuma likitan da ya kware akan ciwon Daddy wanda zai kula dashi a tsahon lokacin da zamu zauna a can. It was almost 8 o'clock pm when we landed a birnin na kasar Germany. Already muka tarar da Uncle Sufyan da dansa Abdul suna jiran saukar mu a airport. Muna haduwa da su Uncle Sufyan ya tarbe ni da murmushi "Safiyya, as beautiful as ever" na sunkuyar da kaina ina murmushi sannan na gaishe shi, duk sanda muka hadu dashi haka yake yi min, ya amsa tare da miƙa wa Daddy hannu at the same time yana cewa "duk sanda na ga Safiyya sai na tuna da Safiya, a rear gem. Har yanzu banga mace irin ta ba. Allah ya kai rahama kabarin ta". Mommy tace "Ameen ya Rabbi. Safiyya is a photocopy of her ai" Daddy ya dago yana kallo na yace "anya kuwa, sunyi kama dai a fuska, amma hali kam basu da dangantaka" na kalle shi muka haɗa ido nayi sauri na mayar da ido na ƙasa. Abu biyu na karanta a idon Daddy a lokacin, akwai grief, wanda duk sanda akayi maganar ta sai na ga yanayin sa ya chanja, wannan yana daga cikin abinda yake kara min fahimtar irin soyayyar da yayi mata, yadda har yanzu, more than 20 years da rasuwar ta, amma bai daina jin mutuwar ta ta ba. Abu na biyu kuma wanda yafi daga min hankali shine disappointment. Daddy was really disappointed in me. Gani yake kamar duk duniya bashi da wani disappointment da ya wuce ni. Naji duk gwuiwowina sun sage, kamar kullum naji babu abinda nake so irin barin duniyar. A lokacin babban concern dina shine Allah ya sa hijab dina ya boye cikina tunda bani da tabbas din hosts din mu sun san da maganar cikin or not. Daga nan muka wuce zuwa inda suka ajjiye motar su, sai da muka je na fahimci cewa motoci biyu suka zo dasu. Daddy ya juyo yana kallona yace "ki shiga motar abdul ya kai ki gidan su ki huta, mu zamu wuce asibiti" na tsaya ina kallon sa idona yana cikowa da hawaye dan naso ace na bishi asibiti anyi komai a gabana, amma kasancewar yanzu bana iya yi masa musu sai nace "okay Daddy". Na tuna da Safiyyan da, da ace seven months back ne, da zan iya rusa kukan da zai tara masa mutane a airport din idan yace ba zan bishi ba. Da ba karamin aikina bane in zauna dirshan a kasa in rike kafafuwansa ina kuka da dukkan karfina, amma yanzu sai nayi taku biyu baya na tsaya ina kallon sa ina kokarin rine kuka na. Ina kallo aka saka Daddy a bayan mota daya, Mommy ta shiga kusa da shi, yaya Mustapha ya shiga gaba sannan Uncle Sufyan ya zauna a drivers seat, aka barni a gefe ina rarraba ido. Mommy ta sauke glass ta ce min "ki kwanta ki huta in kunje, ki sha maganin ki kuma, zan zo gidan in anjima" na gyada mata kai, Daddy kam ko kallo na bai yi ba suka tafi. Sai da motar su ta bar gurin sannan Abdul ya ce min "okay. Daddy's girl. Nasan yanzu zaki kama kuka. Let me take you home tun kafin ki rikice min". Na goge hawayen da ya fito tare da ƙirƙirar murmushi nace "I am not crying" yace "of cause you are not. Maybe someone is cutting onions around". Ya bude min kofar motarsa na shiga sannan ya rufe ya zagaya ya shiga side din driver muka dauki hanya. A hanya yana ta kokarin nuna min gurare amma ni bani da wani interest akan buildings and monuments dinsu, rayuwa ta kawai nake lissafa wa. Har sai da muka yi packing a gaban gidan su sannan ya juyo yana kallona yace "Safiyya, I want to use this opportunity da muke alone muyi magana. Magana nake so muyi as civilized people. Daddy na yace wai sun fara magana da Daddyn ki cewa akwai yiwuwar zasu yi mana aure" yayi shiru yana so yaga reaction daga gare ni sai yaga babu komai, ya cigaba, "so you knows about it kenan. Look, I want you to understand cewa I have nothing against you as a person, I like you. You are very beautiful and intelligent and I am very sure that akwai maza da yawa da suke layi suna son ki zabe su as your life partner. You can have any man you want. Wannan yasa na kasa gane dalilin su Daddy na bullo da wannan maganar. Gaskiya ni dai I don't want arrange marriage. Na fi son inyi aure for love. And I am sure ke ma haka. I know yadda daddyn ki yake son ki ba zai taba yi miki dole ba, and that's why I am begging you. Please idan an tambaye ki kice ba kya sona kamar yadda nima zanyi kokarin nunawa nawa daddyn haka. Let's join hands and fight this battle together. In kika yi min haka I will forever be grateful to you. I am sure kema kina da wanda kike so and I don't want to be the reason da zai saka a raba ku". Na gado kaina ina kallon sa, part of me yana jin dadin cewa bai san maganar cikin jikina ba, part of me kuma was sad that he maybe the one da zan aura and he just told me cewa baya so na. Na ce "I understand. Kana da wacce kake so" yayi murmushi, a lokaci daya na kara fahimta dan na san irin wannan murmushin. Na hadiye wani yawu mai daci ina hango irin murmushin a fuskar Muhammad, wata irin kewar sa tana kara lullube ni, yace "Yes, ina da wadda nake so. Ban ce ta fiki da komai ba but I love her and want to spend the rest of my life with her". Nayi masa murmushi. "I understand. Kuma ina so ka sani cewa nima akwai wanda nake so, so mai tsanani. So in auren mu ya kasance sai dai in kaddarar mu ce haka. But I am not promising cewa Daddy will listen to me because things are totally beyond my control" Na bude kofa zan fita sai na kara da cewa "and I am sorry you are dragged in to this". A gidan su na wuni ranar, mamansa mai kirki wadda dama kullum muka hadu bata da zancen sai na mamana and how close they were kafin rasuwarta. Wannan ya sa I always look forward to meeting her dan insha labaran da suka fi komai daɗi a kunnuwana amma a ranar sai na kasa zama muyi magana nace mata na gaji kwanciya nake so inyi. Ta bude min dakin da na fahimci an riga an gyara shi saboda zuwan mu, ta kuma kai min duk abinda ta tabbatar zan bukata ni kuma na karba nayi mata godiya, sai dai bata amsa ba sai ta bini da kallo kawai, and then I saw a look on her face, a look of disappointment and anger, sai dai bata ce min komai ba ta juya ta fita. But I knew it, a matsayin ta na uwa ta gane ciki ne da ni and she is disappointed in me, and angry at me, because she cared. Na zauna a bakin gado ina jin feeling ɗin da zuwa yanzu na saba da jin irinsa amma kullum intensity ɗin sa karuwa yake yi a zuciyata. Feeling na son mutuwa. Feeling na tsanar rayuwa. Na rufe ido na nayi addu'a a hankali "Allah ka ɗauki rai na a daren yau". Sallolina na tashi nayi sannan na janyo fillow na kwanta na rufe idona tare da fatan bacci zai dauke ni ko na manta da halin da nake ciki, ko da na yan mintuna ne, amma sai dai maimakon bacci sai tunaninnikan halin da rayuwata take ciki ne suka yi ta overlapping kansu a cikin kaina. Har ban san wanda zan dauka daga ciki in duba ba, batun rabuwata da Muhammad ne ko na halin rashin lafiyar da Daddy yake ciki ko kuma na auren da za'a yi min da wanda bana so ko kuma karatuna da nayi asarar shekara uku inayi wannan alakakan cikin da yake jiki na ko kuma tunanin hanyar binciken waye uban cikin ko kuma na vultures din da suka dira akan akaina suke tsatstsagar naman jikina da rai na? Na tashi daga kwanciyar na zauna ina lissafin rabon da inji dan cikina ya motsa tun a Nigeria. Naji wani irin relief a zuciyata "Allah yasa ya mutu" na fada a hankali tare da dora hannuna a saman cikin na dan danna da dan karfi, da karfin shima ya harbo kafa ya doke hannuna, naji wani kulukun bakin ciki ya tsaya min a makogwaro. Sannan na kara number a cikin list na abubuwan da ya kamata inyi tunani akai, "menene makomar abin da yake cikina?" Daddy yace za'a cire shi nan da wata daya da yan kwanaki, amma shi kansa yace bai san yadda zaiyi dashi ba in an ciro shi. Ni kam ko kallon fuskarsa bana bukatar yi and I will definitely not keep it with me. Dan watarana zan iya shake shi cikin dare... Nayi sauri na kawar da tunanin daga raina sannan na koma kan next in line, waye zan zaba a cikin choices din da Daddy ya bani? Definitely not Mustapha. I rather die than in auri Mustapha. And then Abdul dazu ya gaya min da bakin sa cewa baya sona, and bai san da maganar cikin nan ba and I don't know yadda zai dauki maganar idan ya fahimci cewa cikin shege nayi shi yasa a keso a makala masa ni, definitely he will hate me forever. Sai kuma Mukhtar. Mukhtar has been obsessed with the idea of marrying me a cikin shekarun nan. But he doesn't love me. Ni na san abinda yake yiwa, it is the same thing as abinda yasa Mommy take ta nacin a haɗa ni aure da Mustapha, Daddy ma kuma na tabbatar ya sani sai dai kokarinsa na binne abin kunyar da yake ganin nayi ne yasa yake kokarin chosing din su dan yasan zamu juya su suyi abinda muke so dan su samu abinda suke so. Then wanne ne zan zaba daga cikin su kenan? Naji maraici ya sake lullube ni. Babu abinda nake bukata a lokacin illa in samu someone older that I can talk to, wanda zai bani shawara ba tare da wani selfish interest a cikin shawarar ba. Naji ina kewar mahaifiyata kuma ina takaicin rashin sanin kowa a cikin danginta. Na dauko handbag dina na bude na dauko yar karamar purse dina na bude ta itama na dauko wani tsohon hoton katin da nake yawo dashi kullum a cikin jaka. Hoton wata mata ne a zaune akan kujerar gidan daukan hoto irin na kauye, da yara yan mata su uku a jere a bayan ta. Babbar zatayi sheakara goma, mai binta takwas, yar karamar kuma ba zata fi shekaru biyar ba. Duk su ukun da ita suke kama, nima kuma da ita nake kama. Na shafa hoton da hannuna ina lura da yadda duk su hudun suke murmushin da yake nuna yadda suke kaunar junan su, yadda suke cikin farin ciki duk kuwa da talaucin su wanda ake iya gane wa a cikin hoton ta yanayin kayan jikin su. They all had a rough life, a rough ending, but they are all fine now, they are all together now. In Janna insha Allah. Babu kuma abinda nake so a lokacin illa nima in bisu, illa in tafi gurin su. Na dora hoton akan kirjina na rufe ido na sannan nayi kokarin mantawa da komai sai tunanin yadda rayuwar mu zata kasance a Janna tare. A haka bacci ya dauke ni Cikin baccin naji an taba hoton dake kan kirjina. Na zabura da sauri kamar wadda za'a cirewa rai na damke hannun wadda ta dauki hoton. Ido na na shiga cikin na Mommy. Na saki hannun sannan na sauke ajjiyar zuciya na koma na kwanta na mayar da ido na na rufe. Ta juya hoton a hannunta tana kallon mutanen ciki, sai kuma ta zauna akan gadon tana kallona tace "baba Hadiza,  Saudat and the poor little Khadijah. Babu abinda Safiya take magana akai sama da su. They were her inspiration....." "And she is mine" na fada a hankali ido na still a rufe. Tayi ajjiyar zuciya sannan ta mayar min da hoton inda ta dauke shi tace "she is ours. Gabakidayan mu musamman babanku ita ce inspiration din mu. Duk hukuncin da zai yanke a rayuwa sai ya saka interest ɗin ta a ciki. What will she think? What will she say? What will she do? Kullum sune kalmomin sa. Bana kishin ta Safiyya, ban taba jin raina ya baci dan yayi considering dinta ita da bata raye before yayi considering di na ni da nake raye nake kuma matarsa ba, ban taba jin kishi ba, besides ina jin guilt ne na cewa she should be alive, ita ya kamata ta rayu ba ni ba, she should be here enjoying the empire she built with her blood and sweat. But ba haka Allah yaso ba Safiyya, and we can't question hukuncin ubangiji. I will understand if you don't like me Safiyya, maybe irin tunanin da nake yi kema kina irin sa cewa ina living the life that should be safiya's, but I cant wrap my head around the pact that you don't like Mustapha. Me yayi miki shi?" Na bude ido na amma ban kalle ta ba kuma ban ce komai ba. Ta sauko daga kan kujerar ta zauna a kusa dani ta cigaba "Daddy ya gaya min kince ba kya son Mustapha. I won't say nayi mamaki dan tuni na fahimci yadda kike yi masa but I thought kawai kin kasa accepting dinsa ne as a brother ban dauka kin tsane shi bane ba, ban dauka zaki iya putting future din ki da kuma martabar ki in jeopardy kawai saboda mere sentiment". Ta karasa maganar cikin daga murya. Na mayar da ido na na rufe na kuma mayar da hannuna na dora akan hoton kan kirjina. Ina jin ta tana kokarin daidaita muryarta sannan tace "am sorry Safiyya. Am sorry na daga miki murya. Amma ban taba tunanin haka daga gare ki ba. I love you with all my heart Safiyya. Haihuwar ki ne kawai ban yi ba. Idan ke baki sani ba shi mahaifinki ya sani. Soyayyar ki ce ta kawo ni gidan ku. I never expected cewa ke zaki ƙi jini na Safiyya. I never expect kuma daddy zai rufe idonsa ya goya miki. Not after all that has happened" ta sake yin shiru, nima kuma ban bude ido na ba ban kuma yi magana ba. Naji ta kama hannuna ta rike a cikin nata, ina jin yadda natan ya dauki zafi, ta kuma cewa "Safiyya, yanzu duk duniya wa kike tunanin kina da shi da zai rufa miki asiri bayan mu? Wanne family kike da su bayan mu? Ahmad? Kina ganin dai abinda yayi miki a cikin gidan babanki ballantana in kin je gidan shi. Ko kuma Abdul ɗin gidan nan da mahaifiyar sa tun kafin in karaso gidan nan ta kira ni tana tambayar ko abinda ta gani a tare da ke gaskiya ne. Ta yaya kike tunanin zata karbe ki a matsayin sirika? Safiyya idan ma ba zaki yi tunanin yadda zanji a raina in kika yi rejecting jini na ba think of your future and the future if your unborn baby. Think ki gani ina ne kike ganin yafi dacewa da ke". Sai ta saki hannuna ta mike ta shiga toilet. Na bude ido na ina kallon kofar toilet ɗin ina jin zuciya ta babu daɗi, tabbas Mommy tana nuna min soyayya da kulawa dai dai yadda ya kamata, bata taba cutar dani a bayyane ba, not that I know of, bata taba yi min mugunta ba tun ina yarinya har na girma, tun bata san gaskiyar wacece ni ba har ta sani. Sanin nata ya chanja abubuwa da yawa, the changes may be reality or just a pigment of my imagination dan bani da tabbas a kansu. Abinda nake da tabbas akai shine she doesn't deserve a cold treatment from me, Safina ma haka. Mustapha is a different case duk abinda nayi masa bani da nadama amma su dai, especially Mommy ya kamata inyi kokarin kyautata mata ko dan kaunar da take nuna min. Amma kyautatawar ba zata yi involving auren Mustapha ba, in na auri Mustapha da shi zan zauna ba da ita ba and I won't subject myself to lifetime of emotional torture saboda in kyautata mata. Ina kallon ta ta fito ta tayar da sallah nima na tashi na shiga toilet na sake alwala na fito nima na cigaba da sallolina. Sai bayan sallah asuba sannan na hau gado na kwanta bacci mai nauyi ya dauke ni. Cikin baccin naji maganganun Mommy da na Aunty Hajjo suna maganganu, nayi shiru ina son jin me suke cewa sai naji Mommy tace "to har yanzu dai bata fadi waye ba. Ko ta sani ko bata sani ba Allahu a'alam". Aunty Hajjo tace "ikon Allah. Kuma ku bakuyi komai akai ba? Kuka zauna kuka zuba mata ido?" Mommy tace "munyi iyakacin kokarin mu fa, babu abinda bamuyi ba. Munyi running duk options din mu amma ta rufe kowacce hanya da za mubi mu samo wancan yaron da muke zargi" Aunty Hajjo tace "makarantar su fa? Kun bincika ba'a can yaje ba?". Nayi juyi kamar a lokacin na tashi. Mommy tayi gyaran murya sannan tace "ki tashi Safiyya ki ci abinci ki sha magani. Zan koma asibiti gurin Daddy". Na tashi da dan sauri na sannan nace "Mommy zan biki dan Allah. Zanje in ganshi" ta tabe baki kawai bata ce komai ba, da alama har lokacin fushi take yi dani. Na sauko daga gadon na gaishe da Aunty Hajjo, ta amsa da ɗan sakin fuska kadan ba kamar jiya ba amma kuma babu annurin da nakan gani a tare da ita da. Da sauri na shiga toilet nayi wanka na fito jikina lullube da hijab, na debi kayana na koma toilet din babu wanda yayi min magana a cikin su, sai dana shirya na saka wani hijab ɗin sannan na sake fitowa na tarar sai Mommy ita kadai a zaune. Ina zama ta bare magunguna ta miko min tana cewa "na lura in dai bani na baki maganin nan ba ba kya sha Safiyya, ke baki damu da kanki ba ballantana ki damu da wanda ya damu da ke". Na fahimci magana take gaya min amma ban ce komai ba sai kawai na karbi magungunan a hannunta na watsa su gabaki daya a baki na hadiye. Ta tsaya tana min kallon mamaki, ta san da in zan sha magani wani lokacin sai ta kira Safina sun hadu sun danne ni sannan zasu dura min, in sun gama durawa kuma in ba sa'a suka yi ba in yi musu amai a jiki. But now I do not care about anything anymore. Except for Daddy. Ta ce "kinga yanzu ba zama zan ringa yi a gida tare da ke sosai ba. Ki ringa shan magani ko dan ki samu lafiya da karfin jikin da zaki rabu da abinda yake cikin ki lafiya". Na daga kafada "but I don't need it. Daddy yace I won't labour. Za'a yi aiki a cire". Ta saki baki tana kallona, na lura da bacin rai a fuskarta farko ban fahimci dalilin bacin ranta ba sai daga baya sannan na fahimta, Daddy bai gaya mata decision dinsa ba. Ta ajiye robar ruwan hannunta tace "yaushe ne kuka yi wannan shawarar ke da shi?" Na sunkuyar da kaina "ba shawarar mukayi ba Mommy. I thought you knew. Nima gaya min kawai yayi. I am sorry. Zan ringa shan maganin". Ta mike tsaye "ki dauki abinci ki ci ki fito mu tafi. In kuma shima abincin kunyi shawarar ba sai kin ringa ci ba shima sai ki gaya min in daina bata lokaci na akan kokarin baki. Na bar Safina ita kadai a gida, na bar twins a lokacin da suka bukata ta, and I am here a gurin da ba'a bukata ta". Ta juya ta fita da sauri Nima da saurin na hada tea na sha sannan na bita a baya. Ina fitowa sitting room dinsu naga Abdul ya shigo da sauri, yana gani na yayi murmushi "daddy's girl, ke muke jira" ban bashi amsa ba na bishi a baya muka fita. A asibiti muna zuwa muka shiga ciki, Mommy tana gaba ina binta a baya tunda ita tasan gurin. Muka je reception sai naji tana tambayar receptionist din da muka samu a gurin ko an shiga da Daddy gurin aikin da za'a yi masa. Na bude ido ina jin zuciya ta tana bugawa da karfi. Naji matar tace a'a ba'a fara ba an dai yi sedating ɗin sa. Ta nuna mana hanyar da zamu je dakin da aka kaishi. Mommy ta juya zata tafi na tari gabanta da sauri nace "Mommy aiki? Wanne aiki za'a yi masa kuma?" Ta bata rai tace "ba wani major aiki bane ba fa just a minor non surgical operation zasu yi masa suyi clearing airways ɗin sa dan ya samu sauƙin numfashi. I signed the consent yesterday kafin in tafi". Cikin daga murya nace "and why wasn't I informed?" Sai kuma na rufe bakins da hannayena biyu feeling terrible, na kama hannayen ta "Mommy I am sorry, I am very sorry. I don't know menene ya hau kaina, my emotions are all over the place. Please I am sorry" ta dafa hannuna tace "it is okay. I understand. Go and see him". Na juya da sauri mai kama da gudu na tafi dakin da aka ce yana ciki. Ina shiga na ganshi a kwance, flat on hus back, duk da cewa naji sunce allurar bacci suka yi masa amma sai da ganin sa a haka ya tayar min da hankali. Na tsaya ina kallon sa, trying so hard not to imagine ranar da zan ganshi a haka babu rai a jikinsa. Sai naga ya mirsa hannunsa ya bude idonsa ya sauke su a kaina. A hankali naga murmushi ya bayyana a fuskarsa, irin murmushin da yake yi da idan ya ganni. Ya miko min hannunsa "Safiyya. You are here? Zo nan" na tafi da sauri na kama hannunsa da duk hannayena biyu ina jin kamar in tsaga kirjina in saka shi a ciki. Yace "I just had a dream. A very bad dream. Wai wani abu ya faru dake, something terrible. I am glad it was just a dream. I am glad you are okay" sai ya mayar da idonsa ya rufe ya koma bacci. Na kankame hannun sa a kirjina ina kuka "I am sorry Daddy. I am really sorry". Sai da doctors din suka shiga sannan Uncle Sufyan ya fito dani ina ta kuka kamar wani major abu za'a yi masa. Da kyar ya lallashe ni nayi shiru, ina kallon Abdul yana yi min dariya but I didn't find his laughter funny. Sai da nayi shiru sannan Uncle Sufyan yace inzo muje gurin obstetric ɗin da zai ke dubani, I wanted to stay har Daddy ya dawo hayyacin sa amma yace an riga anyi appointment dole inje a ganni. Section daban ya kaini a asibitin, yayi musu magana sai ya tafi ya barni a gurin su, suka dauki duk vitals ɗina da duk wani gwaje-gwajen da ake bukata na masu ciki suka yi recording sannan suka shigar dani gurin doctor ɗin. Shima dai tambayoyin yayi min sannan ya duba duk results din tests din da akayi min. Sai kuma yace in kwanta zaiyi scanning. Na kwanta na rufe idona, ina jin sa yana goga abin scanning din a ciki na amma ban bude ido ba. Naji yace "a healthy baby. As happy as a puppy" sai kuma yayi dariya, ni kuma ban ga abin dariya a cikin maganar ba. Ya ce "will you like to know the gender?" Nayi sauri na girgiza kai na still idona a rufe. Ya sake cewa "open your eyes and look at it" na sake girgiza kaina. Haka yayi ta tsokana ta yana jana da hira dan in saki jiki amma ni ko a jikina. Sai da ya gama na dawo na zauna sannan ya fara yi min bayanin yanayin lafiyar babyn da kuma abinda zan iya fuskanta nan gaba kafin lokacin cire babyn yayi. Ya kara tambaya ta idan da gaske ina son a cire babyn at 7 months na amsa masa da yes, ni da zasu cire shi at 6 ma so nake yi. Har sai da ya gama yace zan iya tafiya, na mike tsaye sai kuma na dawo na zauna ina jujjuya hannu na. Ya tsayar da hankalin sa a kaina yace "is there something you want to talk to me about?" Nayi shiru kamar banji shi ba ina cigaba da jujjuya hannuna sannan na dago kai a hankali nace "when the baby is out. I want to give it up for adoption". Yayi shiru yana kallona fuskarsa da mamaki sannan yace "are you sure? Are you sure this is what you want to do?" Na gyada kaina "I am sure" ya girgiza kansa "I have to talk to your father about this. He didn't mention something like this. I need to....." Nace "I am 21 years old. I am legally old enough to make my own decisions" ya duba file ɗina, maybe to confirm the age, sannan ya sake kallona yace "what about the baby's father. We need to have his approval as well. He needs to.." Nace "there is no father. I don't know who the father is. I was raped" kalmar rape ɗin da na fada ta saka hawaye suka fara bin fuskata, and that caught his attention. Na ga alamun tausayi a fuskarsa, sai kuma yayi dan rubutu a cikin takardu na sannan yace "I am sorry for what happened to you. But I still need you to go home and think deeply about this. If it is still what you want when you come in for your next appointment then we will take the next step. There are papers that you will need to sign. And you have to decide if you want an open adoption or closed adoption. An open adoption is when you leave all your informations so that the baby and it's adoptive parents can keep in touch with you, while a close adoption is when the baby can never be traced to you, you will have no relationship of whatsoever with the baby ......" Direct nace "closed adoption. I want to give up the baby for a closed adoption". Ya cigaba da girgiza kansa. "Please Safiyya, reconsider. Think about this" nace "I have. I have made up my mind. This is what I want". Ya ce "okay. But this is protocol. You have to go and think about it. When you come back next week, then we will finalize your decision". Na gyada kaina. "okay. Thank you" na mike zan tafi, har sai da na bude kofa sai kuma na rufe ina kallon sa nace "one more thing please. I don't want my father to know. I don't want anyone to know. ****. ****. ****. ****. ****. **** Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you…. Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah. [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* Daga marubuciyar: Maimoon A'isha Humaira Diyam Tagwaye Jidda And now..... Safiyya *Episode Five: The Path of Destiny* For sponsorship, contact 0704 203 0419 on whatsap or send a dm to my Instagram page https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ== Save my business number 0704 203 0419 and say hi on whatsap dan inyi saving naku. Please, dan Allah, abeg, ban da kira Ina fita na hango Mustapha yana tsaye a corridor din yana kallon kofar office din da na fito daga ciki, na dauke kaina nayi kamar ban ganshi ba na zo na wuce shi. Ya biyo baya na yana gyaran murya. "excuse me... Akwai mutum fa a tsaye tun dazu yana jiran ki" ban kalle shi ba ban kuma tsaya ba. Ya cigaba da bi na. "Nima bani na kawo kaina ba ballantana ki wulakanta ni. Cewa akayi inzo in jira ki in kin gama in mayar da ke gida, shi yasa na taho ba dan wai ina son hakan ba, kin san ni ina jin maganar Mommy da Daddy in sun gaya min bana tsallake wa". Na tsaya da tafiyar da nake yi na juyo ina kallon sa cikin ido, yayi murmushi, sai kawai na girgiza kaina na juya na cigaba da tafiya a raina nace he is not worth it, so yake in kula shi, in na kula shi kuma na bashi abinda yake so kenan. Ya cigaba da bi na. "excuse me??? Motar tana can side ɗin ba nan ba. You have two options here dear little sister, you can either come with me in kai ki gida kamar yadda iyayen mu suka ce or you can walk tun daga nan har gida, and in your condition, that will be very impossible". Still bance komai ba nayi hanyar inda side din da na bar Daddy dazu. Ya cigaba "okay. You have another option to get home. Maybe zaki samu wani ya baki lift. It won't be hard for you. I mean you are use to it tunda har tsaraba kika samu saboda shiga motar mutane". Na juyo a fusace na buga masa handbag ɗina a kansa, a raina naso ace tana da nauyin da zata ji masa ciwo. Ya dafe kan "aww. Me nayi? Daga fadar gaskiya? I guess ita dama gaskiya daci ne da ita" na juya na cigaba da tafiya ganin yadda mutane suka juyo suna kallon mu. Ya cigaba da bi na yana sosa inda na dake shi. "Kar ki damu. Na yafe miki. Ni bana fushi ai kin sani. Ko da zanyi fushi ma ba zan yi fushi da 'wife' ɗina ba. We will put all these behind us. Now, you will follow me muje in kai ki gida kamar yadda Mommy tace and in turn ba zan faɗa wa Daddy inda kika je ranar nan ba, ba zan bashi labarin me Tesla ɗin nan ba. I guess it won't be hard to trace him with that kind of a car, musamman in akayi considering da rashin girman makarantar ku. I bet shi kadai yake da irin motar a cikin makarantar". Na dakata da tafiyar da nake yi amma ban juyo ba sai da na rufe ido na na ja dogon numfashi da fatan zan hana kaina sauke mari kyakkyawa akan fuskarsa, na juyo da murmushi a tawa fuskar ina kallon sa nace "look Mustapha. Daga maganganun ka na fahimci cewa you are yet to receive the recent memo. Daddy ya fasa aura min kai, because I told him bana son ka. So stop following me around and find a life. And also stop threatening me because it is not going to work". Daga yadda yayi da fuskarsa na fahimci cewa Mommy bata gaya masa ba. Maybe tana fatan zata yi convincing dina na amince da auren so she thought he doesn't have to know. Yace "you are lying. You have always been a little liar" na daga kafada "of cause I am a liar, na sha yiwa mutane da yawa karya, people that matters a lot to me. But I won't waste my time lying to you because you are not worth it. In baka yarda ba ka tambayi Mommy" na juya zan tafi sai dai kuma har nayi taku biyu sai na tsaya na kuma juyowa ina kallon sa nace "and about cikin jikina. Ni na yarda akwai kiyama, na san kuma ni da kai zamu je can. A can ne kuma zamu karasa maganar". Sai da na yi nisa sannan na fahimci baya bina, kuma sai a lokacin na fahimci nayi batan kai na bi hanyar da ba ita ya kamata in bi ba. Sai da nayi tambaya sannan na gane inda na baro Daddy. Ina zuwana tarar da Mommy a zaune a waje. Na karasa gurinta ina haki saboda tafiyar da nayi kuma da sauri. Ta mike tana goge min gumin goshina da hanky din hannunta. "Ya naganki a kafa? Ina Mustaphan da na tura ya dauko ki ya mayar da ke gida ki huta?" Nace "ban san inda yake ba. Ba gida zan je ba. Ya Daddyn? Sun gama?" Ta koma ta zauna tace "eh sun gama. Na gaya miki fa ba wani abu bane za'a yi masa mai wahala ba. Bacci dai yake yi yanzu". Na wuce ta na shiga dakin, na ganshi yana ta bacci kuma ko daga yanayin yadda yake numfashi na fahimci aikin da aka yi masa ya saukaka masa numfashin sosai. Na zauna a kujerar kusa da gadon na kama hannunsa tare da sauke ajjiyar zuciya nace "I love you so much Daddy. And everything is going to be alright" amma ni kaina da na fada sai naji ban yarda da abinda nace ba, saboda a kasan zuciya ta ina jin cewa, this is only the beginning, saboda zuwa yanzu na fahimci cewa "tragedy" is another name for my family. Har dare ina tare da Daddy, duk kuwa da yadda Mommy take ta min maganar tafiya gida amma ban tafi ba na farko saboda bana son tafiya da Mustapha, na biyu saboda ina son spending time a kusa da Daddy duk kuwa da cewa ba kula ni yake yi ba. Sai da daren sannan Daddy da kansa yace ni da Mommy mu bi Uncle Sufyan mu tafi gida, sai a lokacin na sake ganin Mustapha dan tun sa da muka rabu dashi bai dawo ba Mommy ma ina jinta tana ta cigiyar sa. Naga sun tsaya sunyi maganganun su da Mommy sannan ta taho muka shiga mota muka tafi, tunda muka shiga motar kuma bata ce komai ba har muka je gida, da muka je ma bata yi min magana ba sai suka kama hirar su da Aunty Hajjo ni kuma nayi musu sallama na shiga daki. A dakin nayi sallah nayi shirin kwanciya bacci. Kamar kullum ina kwanciya dukkan damuwoyin da nake dasu suka saukar min, amma a daren yau abinda yafi tsaya min arai shine Muhammad. Maganar sa dazu da Mustapha yayi ta taba min bangaren da nake ta kokarin binnewa a cikin zuciyata a kwana biyun nan. Bana son in bude fejin tunaninsa dan bana jin zuciyata zata iya daukan halin da na san yana ciki a yanzu. Na cutar da shi iyakacin cutarwa. Amma kuma bana jin ko da a raina cewa abinda nayi ɗin ba dai dai bane ba. In na gaya masa gaskiya he will stick with me through thick and thin. And I am a walking and breathing tragic bomb waiting to explode. Bana son stains ɗina ya bata white ɗin sa. So nake ya tsane ni tsanar da zata saka ya manta da ni kar ya cigaba da bibiyata. So nake ya samu wadda ta dace dashi yayi aurensa ya gina kyakkyawar rayuwar sa da iyalinsa. Irin kyakkyawar rayuwar da muka fara tsarawa zamuyi ni da shi. Na fara kokarin picturing dinsa ya yanzu, ko me yake yi? Ko yayi bacci? Na duba agogo naga karfe tara, meaning karfe takwas kenan a Nigeria. Na san bai yi bacci ba yanzu. Ten mostly yake yin bacci. A wannan lokacin mostly mukan kasance muna yin waya ne. Na fara kokarin picturing dinsa a dakin sa. Bana jin akwai wani bangare a dakin sa wanda ban sani ba saboda yawan FaceTime da muke yi idan yana dakin. Na tina da wata hira da muka taba yi a cikin irin hirarrakin mu na planning rayuwar mu. ****.     ****.     ****.    ****.    ****.     *** "And you will look so handsome in white" Ya bata fuska "and who told you white zan saka?" Nace "angwaye ai white suke saka wa ranar daurin aure, and I will wear white lace with golden veil and we will snap pictures, irin Mr and Mrs din nan" yayi dariya "ohh Piya, so you think I am like most people da zanyi abinda most people suke yi? I am special. I will wear something special" nace "okay to menene special ɗin, wacce color zaka saka? Pink or yellow?" Ya kyalkyale da dariya, sai kuma ya juya bayansa yana kallon kofa "kinga kin saka ni ina ta dariya a daki ni kadai, kar mutanen gidan nan suce nuts din kaina sun kwance" nace "to ka bani amsa mana. Kasan kuwa har na hango ka ka saka yellow shadda ranar daurin aure?" Ya kuma yin dariya, fuskarsa cike da nishadi dan lokacin bashi da wata matsala a duniya. Nace "am serious fa farar shadda zaka saka" yace "to wai saboda me zan saka fara?" Na turo baki na kwabe fuska kamar zanyi kuka har da bubbuga hannuna akan katifar da nake zaune  "ni dai Allah sai ka saka fara, Allah in baka saka ba ranar kuka zanyi tayi" yace "okay okay shagwababbiyar Daddy. Naji zan saka fara, amma ba shadda ba, sai dai yadi" na danyi tunani sai kuma na gyada kai cikin nuna amincewa "okay. Allah ya taimake ka. Ranar da ka sha rigima" yace "in dai rigimar ki ce ai na saba da ita, in an tashi kawo kayan lefenki har da zanin goyo za'a saka. Dan naga alamar in kika fara wata rigimar sai na goya ki sannan zaki yi shiru". Na rufe fuska ta ina dariya, yace "am serious fa. That's something I can do. I just can't wait for the time". ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    A cikin tunanin bacci ya dauke ni. A cikin baccin ne kuma nayi mafarki da shi. Sai dai a cikin mafarkin ba dariya yake kyalkyalawa ba, in fact fuskarsa a murtuke take da irin kallon da yayi min ranar da muka rabu dashi. Ina tsaye a kofar office dinsa hannayena biyu rike da cikina. "I hate you" ya fada min cikin dacin murya. "I hate you more than I have ever loved you" "You are the worst creature that have ever walked the surface of this earth" Sai kuma ya dauko bindiga daga cikin aljihunsa ya harbe ni da ita a kirji dai dai saitin zuciya ta. Na saki cikin da sauri na dafe kirjin. Ina cewa "I am sorry Muhammad. I am very sorry" Ji nayi an rike kafaduna duk biyun ana girgiza ni da karfi. "Safiyya? Ke Safiyya" da muryar Mommy. Na bude ido na a firgice saura kadan in fadi daga kan gado, sai a lokacin na fahimci, mafarki nake yi, daga alama kuma maganganun da nake yi a mafarkin sun fito fili. Nayi kokarin daidaita numfashina tare da karanto addu'a, sannan na dafe kaina da hannu daya, har a lokacin ina jin amsa kuwwar muryar Muhammad. "I hate you" Mommy tace "wanne irin mafarki kike ne haka Safiyya? Waye kuma Muhammad?" Nayi sauri na kalle ta idanuna a bude. "uhmm Muhamm... Waye Muhammad?" Na mayar mata da tambayar, tace "to ni kya tambaye ni? Ke kike ambatar Muhammad cikin baccin ki kina bashi hakuri" na girgiza kaina "ni ban san wani Muhammad ba. Mafarki ne kawai. Ni ba zan iya tuna mafarkin ma da nayi ba" sai nayi sauri na koma na kwanta tare da jan bargo na lullube har fuska ta tare da rufe idona da karfi ina sauraron yadda zuciya ta take bugawa da karfi, bakina yana furta "innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ni na san a yanzu idan Mommy da Mustapha zasu hada informations din da suke da su a guri daya, to tabbas zasu iya tracing Gidado. And I can't imagine anyi knocking gidan su gidado an gayawa iyayensa cewa yayi wa dalibar sa ciki. Wannan mugun tunanin shi ya yanke min dukkan baccin wannan daren ****.    ****.    ****.    ****.     ****.     **** *Him 👳🏻* Kwanaki biyun nan suna daga cikin worse days of Gidado's life. Gabakidaya kwanaki biyun a daki yayi su, highest da ya fito shine parlor ya gaishe da Abba ya juya ya koma. In an tambaye shi me yake damunsa sai yace bashi da lafiya. Babu abinda bai ce yana damunsa ba. Yace kansa ne yake ciwo yace cikinsa, da daddare kuma da Mama ta shiga har daki ta matsa masa da tambaya sai yace kwakwalwar sa ce take ciwo. It should be funny but it didn't sound funny to Mama, dan sosai hankalin ta yake a tashe akan halin da gudan ranta yake ciki. It also didn't sound funny to Gidado dan shi a lokacin da ya faɗa din har ga Allah ji yake yi da gasken kwakwalwar tasa ciwon take yi, sai dai kuma bai san yadda zai misalta ciwon ba. Zuwa lokaci kowa a gidan ya fahimci halin da yake ciki, zuwa lokacin kuma kowa ya fahimci koma menene yake damunsa yana da dangantaka da Safiyya, saboda dama kowa a gidan ya san da zaman Safiyya ya kuma san da girman matsayin ta a zuciyar Gidado, har Abba. Sai dai duk da cewa sun san abin ya shafe ta amma basu san takamaiman menene ya faru ba, wannan shine abinda Mama take ta tambaya amma ta kasa samun amsa, daga baya dai sai tayi deciding tayi involving dan'uwansa kuma abokinsa, tana saka ran zai iya gaya masa abinda su ba zai iya gaya musu ba. Bayan ta yanke wannan shawarar sai ta kira Al'ameen a waya, wanda yake aboki kuma first cousin a gurin Gidado ta kuma nemi da yazo gidan ya duba halin da dan'uwan na sa yake ciki kuma suyi magana. Da yamma bayan ya taso daga gurin aikinsa ya zo gidan, ya gaishe da Mama ta tambaye shi lafiyar mahaifiyarsa Mami da amaryarsa Humaira, ya sunkuyar da kai yana jin kunya, sai kuma ya mike ya tafi dakin Gidado. Ya shiga ya tarar dashi a zaune akan sallaya ya jingina bayan sa da jikin gado yana jan carbi, idonsa a rufe sai bakinsa da yake motsawa a hankali. Ya zauna a kan kujera yana kallon sa, daga inda yake yana iya lura da yadda idanuwansa suka fada ciki kuma fatar idon tayi baki. "Muhammad" ya kira sunansa. Ya bude idon ya kalle shi sai kuma ya mayar da su ya rufe ya cigaba da jan carbin sa. Al'ameen yayi ajjiyar zuciya yace "ba tun yau ba na gaya maka. That girl is going to be the death of you" Gidado ya kuma bude idonsa yace "congratulations. You predicted right" Al'ameen ya sauko ya zauna a kusa da shi yace "ba haka nake nufi ba, believe me, I cannot say na san exactly me kake feeling right now but I know what loving a girl deeply means" bai ce mishi komai ba sai ya kuma mayar da idon ya rufe. Al'ameen yace "me ya faru?" Yayi shiru bai ce komai ba. Al'ameen ya sake tambaya "did you guys break up?" Gidado ya a girgiza kansa yace "no" sai kuma yayi nodding yace "yes. I guess we did. I don't know" Al'ameen yace "me kake nufi da you don't know. What happened?" Gidado yayi shiru kamar ba zai ce komai ba sai kuma yace "she is.....she said she is.....she told me that she is....... I saw that she is...." Ya hadiye yawu ya kai sau biyar amma kalmomin sun kasa fitowa. Al'ameen yayi kokarin taimaka masa "she is with someone else? She loves someone else?" Gidado ya girgiza kai "no...... Yes. I mean..." Yayi ajjiyar zuciya sannan a hankali yace "I mean she has been with someone else all along. She is married. She has been married all along ". Al'ameen ya bude ido yana kallon sa cikin mamaki. Ya motsa bakinsa amma ya kasa magana. Gidado yace "what a fool I have been" Al'ameen ya girgiza kansa "she is lying. Karya tayi maka. Tana so ta rabu da kai ne shine tayi maka karya" Gidado ya sake girgiza kansa yace "no.... Ba karya take yi ba. I saw it da idona. She is pregnant. I saw her pregnant. She told me she has been married all along" Al'ameen ya gyara zamansa yana kare wa dan'uwan nasa kallo cikin mamaki "kai! Haba! It cannot be. Shekarar ka nawa da yarinyar nan. How can you not know? Ta yaya za'a yi ta iya boye magana kamar wannan" Gidado ya daga kafada "I don't know" Al'ameen ya sake cewa cikin fada "karya take yi fa. Ni nace maka karya take yi fake ciki ta saka a jikinta. There is no way da zaka kasa gane kana tare da matar aure for almost three years. Yadda kuke da ita there is no way da mijinta ba zai gane tana tare da wani ba. My guess is ta samu wani ne and she wants to ditch you shine tayi maka wannan karyar just to break you yadda zaka fi rabuwa da ita" Gidado ya mayar da idonsa ya rufe yana jin ciwon kansa yana karuwa. "I don't know what to believe Ya Ameen. A yanzu haka yaki akeyi a tsakanin zuciya ta da ƙwaƙwalwa ta. Zuciya ta tana son creating all the excuses in the world dan ta kare ta. Ƙwaƙwalwa ta kuma tana kokarin sanin gaskiya. Ni kuma babban abinda nake son sani shine 'why?' idan har da gaske tana da auren me yasa tayi dating dina ta saka min gubar soyayyar ta a cikin jijiyoyin jiki na sannan ta zabi yanzu dan ta watsar da ni. Idan kuma karya take yi kamar yadda kace me yasa zata yi min karyar" Al'ameen ya dafa kafadunsa da hannayensa biyu yace "saboda kamar yadda na gaya maka ta samu wani, someone da take tunanin is better than you. Dama can ba son ka take yi ba". Gidado ya ture hannun sa daga kafadar sa yace "idan akwai abinda nake da tabbas akan shi a cikin duk wannan maganar shine Piya tana so na. I will never believe cewa ba ta so na. Something...." Al'ameen yace "haa.. this is your heart talking. Dan tana son ta. Kamar yadda kace, tana kokarin kare ta ne kawai. How can she love you and then do this to you?". Gidado yace "i don't know. Shine abinda nake ta kokarin sani nima. Shine abinda zan iya sadaukar da komai a yanzu dan in sani. Sai dai bani da yadda zanyi in sani ɗin. Ta toshe duk wata hanya da zan bi in sani, ko kuma at least in ganta, she blocked me" ya fada yana nuna wa Al'ameen wayarsa kamar a jikin screen din ne aka rubuta haka. Al'ameen ya karbi wayar yana kallon hoton jiki yana girgiza kai, a ransa yana matukar tausayin dan uwan nasa saboda yasan zafi da kuma zakin so, ya kuma fahimci soyayyar tayi wa Gidado mugun kamu, sai dai bai yi dace ba. So baiyi masa adalci ba. Ya mika masa wayarsa yace "Muhammadu...... You should stop thinking about how to see or talk to her. You should start thinking about how to forget about her. Mama da Abba are very worried. She is not worth that. Nothing is worth that". Gidado yace "I can't. Ba zaka gane ba Ya Ameen. Ko da zan manta da ita ɗin ina bukatar in san gaskiya. Ina bukatar in ganta mu zauna muyi magana ta fahimtar juna ni da ita. In san ko akwai wani abu da yake damunta.." Al'ameen ya mike tsaye, baya son yaji haushin Gidado amma kuma ya kasa hana kansa. Yace "okay taso muje gidan su sai mu tambaya" Gidado ya kalle shi bai ce komai ba dan ya fahimci bakar magana yake gaya masa, ya sake cewa "ko kuma ka kira wani a cikin yan gidan su kaji abinda yake faruwa. Ko babbar kawarta haka, ai nasan ita ma zata sani". Gidado ya jingina kansa a jikin bango yana jin kamar ya tashi ya shake Al'ameen. Al'ameen yace "ohh haka ne fa. Na manta. Baka san ko daya a cikin wadannan ba. How are you going to know the answers to those questions kuma?". Sai kuma ya dawo ya tsuguna a gaban Gidado yace "look Muhammad, there is no way da budurwar da take son saurayi, so na gaskiya kuma na aure, zata ki kaishi gidan su, zata kuma hana shi sanin kowa nata, for over two years. A cikin biyu dole akwai daya. Ko dai rage dare kawai take yi da shi ba sonsa take ba, ko kuma kamar yadda ta gaya maka, matar aure ce take cin amanar mijinta da kai. I know it is hard Muhammad, but you must see reasons. You must be strong and accept the truth. You must let go ko ba dan kan ka ba ko dan mahaifanka" Gidado ya gyada kai, ba tare da ya bude idonsa ba yace "thank you " Al'ameen ya mike zai fita, har ya kai kofa Gidado yace "Muhammad. Kar ka gaya musu please. Kar ka gaya wa Mama". Sai da yaji alamar ya bar dakin sannan ya bude idonsa yana kallon kofar da Al'ameen din ya fita ta cikinta, amma ba kofar yake kallo ba dan hankalin sa yana can wani gurin daban. Ya dauki wayarsa a gurin da Al'ameen ya bar ta ya kalli hoton kan screen din zuciyarsa taki amince masa da first maganar Al'ameen cewa Safiyya bata son sa tun farko, ba ya jin kuma zai taba yarda da hakan. Ya tuna da rana ta biyu daya sake ganinta a rayuwar sa bayan haduwarsu ta farko a jirgi. Haduwar su ta biyu ta kasance ne shekara bakwai bayan ta farkon. Bayan ya gama first and second degree dinsa ya dawo yayi service. Shekaru bakwai sun wuce amma bai manta da yarinyar da ya taɓa haduwa da ita a jirgi ba. Kuma can a kasan zuciyarsa yana fatan zai kuma haduwa da ita. ****.     ****.    ****.    ****.    ****.     **** A hankali yake tafiya a motar sa, yana juya stirring cikin nutsuwa zuciyarsa cike fal da farin cikin da bai san dalilin sa ba, amma yana tunanin akan maganar da suka yi da Abba ne dazu. Ya kunna kida kadan kadan yana tashi yana kara masa nishadi, a ransa yana lissafa rayuwarsa and how successful everything has been going for him.  Yayi dialing number ɗin abokinsa da ya fito nema "kai ya? Gani fa a junction ɗin, ina zan juya" abokin yayi dariya yace "kai fa matsala ta da kai baka san gari ba. Abeg I can't direct you, ask Google map" ya katse wayar. Gidado yayi dan karamin tsaki "karamin dan is, sai in fasa zuwa ma" ya cigaba da driving a hankali da hannu daya dayan hannun kuma yana kokarin nemo direction din inda zai je. Ya dago kai dan tabbatar da inda yake. A lokacin ne ya ganta. Tana tsaye a gaban mota hannunta daya rike da key din mota dayan kuma rike da jakarta. Fuskar ta a murtuke da alamar bacin rai. Ga uwar ranar da ake kwallawa a ranar. Kallo daya yayi mata ya dauke kai ya cigaba da abinda yake yi, har motar sa ta gota inda take sai kuma ya dago kai da sauri ya sake kallon ta ta mirror din motar. Gabansa ya fadi yana ganin kamar yasan fuskar. Yayi slowing down ya sake gyara mirror dinsa dan yana kare mata kallo. Yaji wani excitement ya shige shi. Komai na features din fuskarta suna nan kamar yadda yake tuna wa da su but more matured, no longer child like but lady like. More feminine. More beautiful. More beautiful than he had ever imagined she would be. Ya tuno da ranar da suka hadu a cikin jirgi. Surutun da ta ringa yi masa, tsokanar sa da ta ringa yi, da kuma yadda suka rabu. Ita ta riga shi fita daga jirgin a ranar dan air hostess ce ta dauko mata jakarta daga inda ta barta ta taho gurinsa, ta kuma zo suka fita tare. A arrival yayi ta baza idon ko zai sake ganin ta amma bai ganta ba. He then wondered ko paths dinsu zasu sake crossing later in life. And it did ... Sai dai kuma bashi da tabbas din zata ma tuna da shi ballantana har ta gane shi. Yayi reversing motar a hankali still yana kare mata kallo dan ya tabbatar da cewa ita din ce dan kar yaje yayi wa wata magana. Sai dai yana zuwa saitin ta sai ta kara yin gaba kamar bata san mota ta tsaya a gaban ta ba. Ya bude kofar motar ya fito still idonsa a kanta. Yana jin zuciyarsa wani iri dan shi dai bai taba ganin macen da ta yi masa kyau kamar ta ba, bai kuma taba tsayar da mace a hanya yayi mata magana ba. Ta ƙara bata rai tare da juya fuskarta daya side ɗin, daga alama kallon da yake yi mata ya dame ta. Ya tako zuwa gabanta, sai ta zaro wayar ta ta fara dannawa kamar bata san dashi a gurin ba. Yayi mata sallama. "Assalamu alaikum" ta amsa, amma shi kansa da yake kusa da ita motsawar bakinta kawai ya gani amma baiji muryar ta ba. Ya danyi shiru yana tsoron kar ta wulakanta shi amma kuma yana son gwada sa'ar sa, ya dan leka fuskarta a hankali yace "Piya?" Ta dakata da danna wayar da takeyi ta dago kai tana kallon sa da alamar tunani a fuskarta, lokaci daya kuma sai yaga recognition a fuskarta, and farin cikin da yaji a ransa was more than he thought. "Malam Muhammadu dan fillo?" Yayi dariya, dariyar da yaji ts wanke dukkan tsoronsa. Ta nuna shi da dogon yatsan ta "Washington DC" ya girgiza kai "no. Manchester" tace "yeah. Right. Manchester. What are you doing here? How are you here?" Yace "ke zan tambaya. Never thought I will ever see you again" tace "me too. It has been five years?" Yace "seven" tace "wow. How time flies. Kayi girma sosai" ta fada tana kallon sa tun daga kan takalmin kafarsa har zuwa yalwatacciyar sumar kansa da bai rufe da hula ba. Ya shafa kansa "ke ma haka". Suka yi shiru duk su biyun, kowanne su trying not to look at the other. Sai kuma suka kalla a tare, suka hada ido, and then they smiled together. "uhmm ...... Trouble with the car?" Ya tambaya yana nuna motar da take tsaye a gabanta. Ta bata fuska "wallahi... Ta mutu.... I don't know why. Ina tafiya kawai ta mutu. Na kira kuma an hada ni da mechanic har yanzu kuma bai zo ba" yace "why not leave the car here in yazo ba sai ya dauka ba. You shouldn't be here standing under the sun" ta daga mishi key din motar "sai yazo zai karbi key ai" ya girgiza kai "still sai yaje gida ya karba. You shouldn't be here alone" tayi ajiyar zuciya bata ce komai ba. A hankali yace "can I take you home?" Ta juya ta kalli motar ta, sannan ta kalle shi fuskarta kamar zata yi kuka, yace "sai in dawo wa da mechanic ɗin key din, in bai zo ba kuma I can get another one for you" ta girgiza kai "ba wannan ne damuwa ta ba. Uncle Ahmad will kill me today. Yace kar in fita da mota. Yace ban iya mota ba. Baya son a bani mota ni kuma so nayi in nuna masa na iya" Gidado ya mika mata hannu yace "mu ga key din" ta bashi, hoping motar lafiyar ta kalau itace dai bata iya din ba. Ya bude ya shiga yayi ƙoƙarin tayar da ita amma sai yaji yana murda key din tayi wata irin kara. Ya fito yana kallon Safiyya yace "key starter din ta ta lalace. Maybe kinyi ta murda key din ne" ta fara bubbuga kafa a kasa "to ba ita ce taki tashi ba" yayi dariya "tuba take yi. Now call the mechanic and tell him key starter issues ne, tell him kuma zaki tafi gida yazo gida ya karbi key ɗin". Tayi abinda yace sannan ya bude mata passenger's seat din motarsa ta shiga ta zauna shi kuma ya zagaya ya shiga seat din driver. Suna kama hanya ya lura duk ta zama uncomfortable, sai yayi kokarin yi mata hira "you look good. You look really good" ta danji kunya "thank you. You too" yace "so... how have the 7 years been going?" Tayi ajjiyar zuciya "like the blink of an eye" yace "na dauka ba zaki gane ni ba fa, I was praying kar ki yarfa ni" tace "nayi niyyar yin hakan fa. But sai kuma ya kasance kai ne. Ni ma nayi mamaki dana gane ka. Amma kai ya akayi ka gane ni?" Ya daga kafada "ina da saurin gane mutane. Besides, I have thought about you a lot within these years. Ke fa" tace "ina tuno da kai ne kawai idan na shiga jirgi na hadu da me aerophobia" suka yi dariya a tare. Wayarta tayi kara, ta dauka. Shi kuma ya samu damar cigaba da kare mata kallo "Yaya Mukhtar na bar gurin fa. Na kira shi nace ya same ni a gida. Alright. Don't tell Uncle please. Thank you". Ta ajiye wayar tare da ajjiyar zuciya yace "I like the way you talk" ta juyo tana kallon sa tace "what?..." Ya maimaita "I like the way you talk. I am not sure if it is the way your lips moves or the sound of your voice or the body language, ban sani ba. I just like it. It is therapeutic" ta sunkuyar da idonta kasa tana murmushi, ya kara da cewa "and the way you smile too". Sai ta ja mayafin ta ta rufe fuskarta. Ya tsaya yana kallon dogayen yatsun hannunta. Aka kira wayar sa, ya dauka direct yace "kai na fasa zuwa fa. And don't call me again". Ta bude fuskar ta tana murmushi tace "babu kyau karya alkawari fa" yace "ba alkawari nayi ba  fa. Besides, there is no where I would rather be then here". Motarsa ce tayi wata yar kara sannan ta mutu. Suka juya suka kalli juna. Yayi kokarin sake tayar da ita amma taki tashi. Safiyya ta rufe fuskarta tana dariya yayin da shi kuma ransa in yayi dubu ya baci. Ta bude fuska tace "it is official. Yau da rashin sa'a na tashi" ya juyo yana kallon ta yace "ni kuma yau sa'ar dana tashi da ita bata ma misaltuwa". Tace "I am not sure. Maybe this is a sign that we are not meant to be together" ya bude kofa ya fita yana girgiza kai da sauri. "No. This is a sign that we will walk the path of Destiny together" ta fito itama tace "walking? Not driving" yace "I am ready to do it if you are" ta saka hannu tana kare rana tace "under the sun?" Ya zagayo gaban ta ya tsaya, jikinsa yayi blocking mata hasken rana yace "I will shield you". Suka fara tafiya a hankali, side by side, enjoying each other's company, breathing in each other's scent, suna kuma updating juna akan abubuwan da suke faruwa a rayuwar su. A lokacin ne ya gaya mata karatu dama yaje yi Manchester, kuma ya gama degree dinsa na daya dana biyu, ya kuma yi service. Ya kuma sanar mata da bukatar mahaifinsa akan yaje yayi aiki a ƙarƙashin sa, da kuma shi burinsa na yayi aiki a sabuwar jami'ar da baban masa da siblings dinsa suka bude in memory of mahaifinsu ambassador Muhammad Dikko, M.D University Abuja "ina so nima in bayar da tawa gudummawar wajan kafa jami'ar". Ta fahimta, sannan itama ta bashi nata labarin. Family dinta mazauna garin Kano ne. Ta gama Sec school dinta three years back, amma kuma sai babanta ya fara rashin lafiya. Jinyar sa ya saka bata fara jami'a ba saboda basa zama a kasar ko da yaushe suna yawon kasashe neman magani, sai yanzu ne yayi insisting dole ta dawo Nigeria ta zauna a gidan Uncle din ta anan Abuja ya nema mata admission a daya daga cikin manyan private universities ɗin da suke garin. Last week ta zo garin. Kuma already ta gaji da garin. A lokacin suka kai karshen junction ɗin suka hau kan babban titi. Suka tsaya suna kallon juna yace "we did it. The path was rough, tiring and very sunny. But we arrived at the destination, together" Kafin tayi magana mota ta tsaya a gabansu. Aka sauke glass din wani ya leko "Fiyya. There you are. Na kasa hakura shine na biyo bayan ki. Let's go home kafin ya dawo ya ga bakyanan" tayi ajjiyar zuciya, daga alama ranta bai so haka ba. Ta so su ci gaba da tafiya a kafa ita da shi. Duk da dai cewa a kwai wahala, but with him by her side, zata jure. Ta juya tana kallon Muhammad tace "cousin dina ne. Gidan su na sauka. Kafin kazo dazu shi na kira na gaya masa inda nake" Ya gyada mata kai "go" tace "okay. Zamu yi magana" yace "yes. I will call you" ta danyi shiru tana kallonsa. Ya sake ce mata "go... Rana tana dukan ki. It is not good for your skin" tayi murmushi. Ya bude mata kofar motar. Har zata shiga ta kuma juyowa tana kallon sa tace "are you not forgetting something?" Yayi shiru yana tunani sannan yace "no. Me na manta?" Tayi murmushi tace "I don't know. Kawai ji nayi kamar kayi wata mantuwa" na motar ya leko. "common. Let's go sauri nake yi fa" ta shiga reluctantly ta zauna, Gidado ya ja baya tare da yi mata alamar I will call you. Ta yi murmushi. Sai da motar tasu ta ja sannan hankalin sa ya dawo jikinsa. Sannan ya fahimci abinda take cewa ya manta. "God damnit" ya fada da dan karfi. "Damnit" Ya maimaita yana saka yatsun hannunsa duk goman a cikin gashin kansa yana jin kamar ya fincike gashin ya zubar. Bai karbi number wayar ta ba. ****.    ****.    ****.     ****.    ****.    ****.    Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you…. Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah. [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* Daga marubuciyar: Maimoon A'isha Humaira Diyam Tagwaye Jidda And now..... Safiyya *Episode Six: Mother* For sponsorship, contact 0704 203 0419 on whatsap or send a dm to my Instagram page https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ== Save my business number 0704 203 0419 and say hi on whatsap dan inyi saving naku. Please, dan Allah, abeg, ban da kira Free page...... Knocking kofa ne da dawo dashi daga tunanin da yake yi. Ya mike ya koma kan kujera ya zauna yace "yes". Mama ce ta turo kofar amma sai ta tsaya daga bakin kofa tana karewa dakin kallo tace "ina Al'ameen ɗin? Ko ya fita bai yi min sallama ba" Gidado yace "ya fita, maybe ba kya kusa" ta karasa shigowa da bacin rai a fuskarta tace "ko bana kusa ai sai ya neme ni, saurin me yake yi? Ni fa na kira shi kuma sai ya tafi ba tare da na sallame shi ba" Gidado bai ce komai ba amma ya san shi ya jawowa Al'ameen wannan fadan tunda shi yace kar ya gaya mata maganar da suka yi, ya san kuma Al'ameen ya gudu ne dan baya so ta tambaye shi ya suka yi. Ta shigo ta zauna akan gado tana kallon sa tace "ya jikin?" Ya ajiye carbin hannunsa tare da safa addu'a a fuskarsa yace "da sauki Mama, kar ki damu da ni. Zan je asibiti anjima" ta bata rai "in kaje asibitin me zaka ce musu? Ji nake dazu da na tambaye ka abinda yake damunka cewa kayi kwakwalwar ka ce take ciwo, haka zaka ce musu a asibitin? ta yaya zaka ce kar in damu? Ki yadda ka koma cikin kwana biyu, me yasa ba zan damu ba? Akan ka aka fara faɗa da budurwa ne wai?" Gidado ya dago kai yana kallon ta, ya bude baki sai kuma ya mayar ya rufe. Shi bai san me zai ce mata ba. Baya son ya gaya mata abinda ya faru tsakanin sa da Safiyya saboda baya son ta tsani Safiyyan, duk kuwa da cewa bata san ta ba. Wannan shine zurfin soyayyar da yake yi mata. Yin shiru sa ya saka ranta ya kara baci. "Kai ba zaka gaya min ba kuma shima dana turo ya tambaye ka ya tafi bai gaya min ba. Wani abu ne mai muni ya faru? Ko wani laifin ka aikata kake boye min?" Yayi saurin girgiza kai tare da bude ido "no, Mama babu abinda nayi fa. Babu abinda ya faru, kawai bana jin dadi ne. Kuma zanje asibiti in an jima". Ta dauki wayarsa daga kasa ta mika masa tace "idan har babu wani abu da ya faru kira Safiyya ka bani ita mu gaisa" ya rike wayar yana jujjuya ta. "Bata kasar, kiran ba zai shiga ba" tace "WhatsApp call nko? Shima ba zai shiga ba? Ko kuma da ta tafi wata kasar a matsayin ka na mai neman aurenta bata baka layin da take amfani da shi a can ba?" Ya ajiye wayar akan cinyarsa tare da sunkuyar da idonsa kasa, abubuwa da yawa suna yawo a ransa. Ta kuma daukan wayar and kafin ya fahimci me yake faruwa sai ta kama hannunsa ta saka fingerprint dinsa ta bude wayar. Ya dago kai da sauri yana kallon ta, trying to process abinda yaje faruwa "Mama! Mama Please don't!" Ta juyo tana kallon sa tace "ko zaka kwace wayar ne? Ko kuma akwai abinda kake boyewa ne wanda baka son in gani? I cannot just seat idle and watch you turn into this, sai dai in abinda yafi karfina ne". Yayi shiru tare da saka hannu biyu ya dafe kansa, shi dai yasan babu wani abin ashsha da yake cikin wayarsa wanda ba zai iya budewa a gaban ta ba, abu daya ne baya so ta gani wanda kuma ya san shine abinda take after, chats dinsa da Safiyya. Tun shekaran jiya Safiyya tayi blocking din calls dinsa, amma kuma ta manta bata yi blocking dinsa a WhatsApp ba, wanda dama shine kadai social media app din da yake yi anan ne kuma suka fi yin hira. Tun shekaran jiyan kuma yake tura mata sakonni, amma ya fahimci kamar data dinta a kashe take gaba daya dan sakonnin basa zuwa gare ta, amma hakan bai hana shi rubuta wa ba, hakan bai hana shi gaya mata duk abinda yake zuciyarsa ba, all the things that he wanted to say to her, hoping that zata bude ta karanta ko da ba yanzu ba ne ba. Ya tabbatar kuma idan Mama ta karanta sakonnin zata fahimci gaskiya abinda ya faru tsakanin sa da Safiyya, zata fahimci cewa Safiyya matar aure ce kuma har tana dauke da ciki. Bata jima tana danna wayar ba kuwa ta ga abinda yake boyewa, tun daga expression din fuskarta ya gane ta gani.  Da sauri take karantawa harshenta har yana hardewa. Wadansu maganganun a fili wasu a zuciyarta. Har tazo kan wanda ya warware mata warware mata damuwarta ya kuma ɗora mata wata damuwar data ninka waccan. "I only want to know me yasa kika yi min haka, me nayi miki da zaki yi min haka, how can you let me fall this deeply in love with you alhalin kina matar aure?" Mama ta saki wayar daga hannunta ta fadi akan carpet, "Muhammad!" Ya jawo hannayensa daga kansa ya rufe fuskarsa da su yana jin wani zazzaɓi mai zafi yana saukar masa. "Matar aure fa Muhammad. Yanzu Gidado dama da matar aure kake tare? Matar wani?" A muryar ta yana jin irin zafin da yake zuciyarta and how much disappointed she was in him. Ya zame daga kan kujerar ya sauko kasa "Mama.... Mama wallahi..... Na rantse miki wallahi ban sani ba" ta mike tsaye sannan ba tare da tace komai ba ta yi hanyar fita. Ya mike shima ya bita a baya da sauri "Mama, Mama" bata waiwayo ba har suka zo suka wuce Mufida a falo , Mufida ta bisu da kallo cikin tunanin abinda ya faru, har sai da ta shiga dakin ta sannan ya samu ta juyo ta kalle shi, sai dai ganin hawaye a idonta ya saka ya ji kafafuwansa sun kasa daukan sa. Ya zame ya durkusa a gabanta "innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Mama dan Allah kar kiyi kuka a kaina. Wallahi ban san tana da aure ba. Boye min tayi" ta juyo da tsawa tace masa "ka tashi ka fita ka bani guri, ka tashi in daina ganinka a gaba na kar kasa inyi maka abinda ni da kai gabakidaya zamuyi nadama" ya mike da sauri ya fita, ta turo kofa ta rufe, amma sai ya kasa tafiya ya jingina da jikin kofar sannan ya zame ya zauna a gurin, babu abinda bakinsa yake furta wa sai innalillahi wa inna ilaihir rajiun, shi kansa ya kasa tantance me yake faruwa da rayuwarsa, a cikin kwanaki biyu rayuwarsa ta juya daga good zuwa bad and now it has turned to terrible. Tun tasowarsa he has always been Mama's boy, akwai shakuwa da fahimta sosai a tsakanin sa da ita. She raised him and his siblings with love, da soyayya ta raine su da soyayyar kuma ta tarbiyyan tar da su. Tun tasowarsa kuma ba zai iya tuna ranar da ya ganta cikin bacin rai irin na yau ba. He has always been a good boy. Da wahala yayi laifin da zata daga masa murya ma ballantana har ta kai ga zubar da hawaye a kansa. Ya tuna da maganar da Ya Ameen ya fada masa dazu, cewa Safiyya is not worth bacin ran iyayensa, a lokacin maganar bata dake shi sosai ba sai yanzu da yaga bacin ran na gaske. Yana nan zaune har Mufida da ta ji su shiru ta taso ta biyo bayansu, a lokacin ne ta ganshi a zaune a kasa a kofar dakin Mama, hankalin ta ya tashi dan bata taba ganin yayan nata a cikin irin wannan halin ba. Ta durkusa a gabansa tare da dafa kafadarsa "Hamma? Lafiya? Me yake faruwa?" Ta fada muryar ta tana rawa kamar zata yi kuka. Ya dago jajayen idonsa yana kallon ta yace "Mufida. Kiyi min addu'a. In kinyi sallah kiyi min addu'a" ta rike kukan da yake neman kwace mata tace "kullum ina yi maka addu'a dama Hamma, amma yau zan tashi cikin dare zanyi sallah musamman dan kai, zanyi maka addu'a, insha Allah Allah zai yaye maka dukkan damuwarka". Ranar cin abincin daren su sam bai yi armashi ba a gidan. Dan yau damuwar Gidado tafi ta kullum yawa, Mama ma kuma juya abincinta kawai take yi ba ci take ba. Daga baya ma sai ta tashi tace musu zata je ta kwanta. Gidado ba haka yaso ba, so yayi tayi masa fada, so yayi ta gayawa Abba in yaso sai ya samu damar yi musu bayani tare da kare kansa, amma maimakon haka sai ta bashi silent treatment. Kwanan su biyu a cikin wannan yanayin. A rana ta biyun ne Gidado ya samu Mama a kitchen tana aiki tare da Mufida ya ajiye mata wayarsa. "Mama dan Allah in ba zaki saurare ni ba ma fa wayar tawa nan ki duba, ki karanta sakonnin gabaki daya zaki fahimci gaskiya ta" ta juyo ta kalle shi, zuciyarta tana yi mata zafi akan yadda dan lelen dan nata ya koma saboda mace, tace "bana bukatar duba wayarka, na riga naga abinda nake bukatar gani. Kaje kawai, zanyi addu'a akan ka zan kuma yi tunani, sannan zan gayawa mahaifinka halin da kake ciki dan ya damu da ya sani, abinda duk muka yanke a kanka kuma dole shi zaka bi". Ya gyada kai cikin amincewa. Shi indai zata daina fushi da shi to kowanne hukunci ne ya yarda zai dauka. Washegari ya fahimci cewa ta gaya wa Abba abinda ya faru, dan sanda ya gaishe shi bayan sun dawo daga masallacin sallar asuba kin amsawa yayi, rana ta farko a rayuwarsa daya gaishe da mahaifinsa bai amsa masa ba. Wannan ya sa a ranar ko dakinsa bai koma ba anan falo ya kwanta anan falon yana jiran Abba ya shirya ya fito ya sake gwada sa'ar sa ko zai samu ya kula shi, yayi masa fada, kai ko dukansa ne ma ya yarda yayi in dai zasu daina fushi da shi. Yana nan kwance Mufida ta fito, yaji tazo tana taba wuyansa sannan ta koma suka dawo tare da Hafeez, yana ji suna ta maganganun su sannan Hafeez din ya tafi suka dawo tare da Abba. Yaji Mama tazo itama. Ya tashi zaune yana jin sanyin acn falon tayi masa yawa a jikinsa. Abba ya aika Mufida yace ta kawo masa abinci daga nan kuma sai ya sallame su ita da Hafeez. Gidado ya dauki cup din tean da aka ajiye a gabansa ya kai bakinsa amma bai kurba ba sai ya ajiye shi, pretending kamar yasha. Mama tace "dauki ka shanye" babu musu ya dauki kofin ya shaye tas duk da kona mishi baki da yake yi. Abba ne yayi magana yace "mamanka ta bani wani labari da ban taba tunanin jinsa ba. Tace min yarinyar da kake ta maganar za'a je nema maka auren ta, Safiyya, matar aure ce, haka ne" Gidado ya gyada kai, har lokacin zuciyarsa ta kasa sabawa da jin sunan Safiyya tare da kalmar matar aure a hade a sentence daya. Abba yace "to me zaka ce game da haka?" Gidado yayi gyaran murya yace "ban san haka bane ba. Sai last gani na da ita take gaya min hakan" mama tace "take gaya maka me?" Yace "tace min..... Tace she is married". Abba ya gyara zama "amma kai tun da kuke da ita ba ka taba gane cewa matar aure ba ce ba? Ta yaya? Kana me zata ninke ka a baibai tsahon lokaci baka gane ba? Wanne irin so kake mata da zai rufe maka ido from the obvious?" Gidado yace "Abba ban san ya zanyi bayani ku gane ba. Da ace kun santa zaku fi yarda da magana ta. Babu wani alamun aure a tare da ita. Ban taba zuwa gidan su ba ballantana in gane daga nan...." Mama tace "baka taba zuwa gidan su ba? All these while har ka yi gini ka saka ni hada kayan lefe amma baka taba zuwa gidan su ba?" Gidado ya dafe kansa "how foolish he might have looked a idon iyayensa, how foolish duk wanda yaje abinda ya faru zai dauke shi, amma kuna it is easy to judge idan har abin bai faru da mutum ba. Yace "Mama, Safiyya student ce a MD, a hostel take zaune, asalin iyayenta yan Kano ne, mahaifinta ba mazauni bane kusan ko da yaushe baya kasar. Duk sanda akayi hutu itama tana binshi whichever kasa yake a lokacin. A cewar ta kullum tana kokarin samun chance idan yazo gari ta kaini. Tace bata son kaini gurin kaninsa, wanda yake zaune a garin nan, tafi so in ganshi direct because of some family issues that she didn't mention. I didn't push sosai saboda baban bashi da lafiya, kusan ko da yaushe yana asibiti. She ......" Mama ta katse shi "wannan shine abinda ta gaya maka? To bara in gaya maka gaskiyar magana. Babu wani gurin babanta da take zuwa. My guess is gurin mijinta take zuwa in anyi hutun. Yana kasar waje ita kuma tana nan tana karatu, in anyi hutu kuma ta tafi gurinsa. In ta dawo kuma kai gaka. Ta jefi tsuntsu biyu da dutse daya". Gidado ya rufe idonsa yana tuno hotunan Safiyya da Daddyn ta, most of them a asibiti, ya girgiza kansa, baya son yayi tunanin abinda zuciyarsa take hasaso masa. Abba yace "to a karshe kuma ya akayi ka sani?" Ya bude idonsa yace "taje holiday kamar yadda ta saba, and she have been acting off for months, she came back tace tana son ganina, muka hadu a office dina, and she told me". Abba yace "and kai me kake tunani? Do you believe she is really married ko kuma she is lying tana so ne dai kawai ta rabu da kai?" Gidado yayi shiru because that was a million dollars question, bai san amsar ba, zai kuma iya bayar da komai dan yasan amsar. Cikin jikinta shi yake convincing dinsa akan cewa tana da aure din, amma kuma yanayin yadda tayi masa magana, da abubuwan da suka gudana kafin ranar, suna so su gaya masa cewa da akwai wata a kasa. Amma ya kasa fahimtar if those things are real ko kuma zuciyarsa da take cike da sonta ne take imagining dan ta bata kariya kamar yadda Ya Ameen ya gaya masa. Ya dago kai yana kallon Abba yace "I don't know Abba. I don't know what to think. I don't know what to believe " yayi shiru kuma sai yayi deciding ya gaya musu all he knows, idan akwai wanda zai taimaka masa kaf duniya to su ne. Sai ya kara da cewa "she is pregnant". Da sauri Mama tace "ita ta gaya maka?" Yace "gani nayi" tace "to wannan shine dalili, ta gaya maka gaskiyar ita matar aure ce saboda cikin jikinta. Shi ciki ai ba'a boye shi. Bata yi niyyar fada maka ba sai data tabbatar in bata fada ba ma zaka gani da idonka" Abba ya gyada kai cikin amincewa sannan yace "that will be all. Tashi kaje". Gidado ya mike, a ransa yana jin mix feelings. Na farko yana jin dadin iyayensa sun fahimce shi duk da dai har lokacin suna ganin da laifin sa a ciki, amma kuma yana jin babu dadin yadda suka dauki maganar, a gurinsu a yanzu babu halitta worst than Safiyya. Yana rufe kofa Abba ya juyo yana kallon Mama da bacin rai a fuskar sa yace "da ace nasan wacece yarinyar nan da ta mayar min da ɗa haka wallahi da sai na san waye uban ta a Nigeria" Mama tayi murmushin takaici tace "she can be traced, tunda daliba ce a MD, shima kansa Gidadon zai iya tracing danginta idan yayi niyya but to what end? Menene amfanin hakan? Allah zai saka masa kawai. What we should concentrate on a yanzu shine ganin ya dawo hayyacin sa". Ya gyara zamansa yace "abinda muka yi magana akai kawai shine" tayi ajjiyar zuciya tana girgiza kanta. "I don't know dear, what works for some might not work for others. Aure kuma is a life sentence. Bana son garin neman gira mu rasa ido". Ranar Gidado wuni yayi da wayarsa a hannun sa. Ya daina kiranta ya kuma daina tura mata messages amma wuni yayi yana kallon pictures da videos dinsu together, trying to figure out a ina hint din cewa tana da aure yake, trying to see beyond the obvious amma babu abinda ya gani sai soyayya, tsantsar soyayya. A karshe sa yaji kamar zuciyarsa zata fashe sai ya rufe wayar ya kuma rufe idonsa, a haka bacci ya dauke shi, cikin baccin ne yayi mafarki da Safiyya a tsaye a kofar office dinsa hannayenta biyu rike da cikinta, hawaye sharkaf a fuskar ta, ta mika masa hannu daya tana kiran sunan sa "Gidado please, I am sorry. Muhaammaaad...." Yayinda shi kuma ya saka hannu biyu ya hankada ta waje sannan ya rufe kofar. *Her* 🧕🏻 Kwanaki ukun nan sun wuce wa min very slowly. Bawai ina ganin rashin saurin kwanakin bane saboda kasancewarsu event-less, a'a, abubuwa ne da yawa suke faruwa not one after the other but all at the same time, abubuwan da suka cika min kwakwalwa ta har suka sa ka bata gane komai. Mommy ta saka ni a gaba da zancen auren Mukhtar, Mukhtar ya takura min da kokarin chanja min ra'ayi a kansa, Abdul ya cigaba da rokon na akan kar na zabe shi a matsayin miji, yayin da Daddy ya cigaba ta tambaya ta akan wanene zabina. Ni kuma a gurinta zancen aure shine least of my problems, babban matsalata shine lokaci yayi sauri yazo a raba ni da cikin jikina ko na samu freedom ɗin da zan ji daɗin jinyar Daddy, ko hakan zai bani damar rekindling relationship din mu. Sai dai kuma shi Daddy kullum maganar sa ita ce "bana son in tafi in barki a wannan yanayin Safiyya. So nake in gyara rayuwarki kafin in tafi in barki". And through all these, Gidado weight heavily in my heart.💜 Tunanin halin da yake ciki ya kara wa wuni na tsaho, mafarke mafarken sa kuma sun hana min bacci mai nauyi. A ranar da muka kwana biyar a garin ne na samu nayi dogon bacci da safe irin wanda na jima ban yi irin sa ba. Har Mommy ta tashi ta shirya ta tafi asibiti gurin Daddy ta barni bacci. San da na farka na danji dadin jikinta sosai, dan rashin baccin ma yana daya daga cikin abubuwan da suke toshe min tunanina. Na tashi nayi wanka na fito ina shirya wa ina tunanin yadda zan kai kaina asibitin tunda babu kuɗi a hannuna dan tunda muka zo ban yi chanjin kudi ba. Na zauna tana lissafe lissafen abun yi sai ga Aunty Hajjo ta shigo dakin. Na gaishe ta ta amsa sai naga ta samu guri ta zauna akan kujera, wannan ya saka ni feeling uncomfortable na sunkuyar da kaina, hoping cikina bai fito sosai ba. Sai naji ta fara magana "Safiyya dama ina ta so muyi magana da ke amma bana samun damar kasancewa da ke ke kadai, kuma maganar da zan yi miki da ke kadai nake son yinta. Na cigaba yin shiru ban ce komai ba, ta cigaba "Sa'adatu ta bani labarin abinda ya faru dake, ko kuma ince abinda ke kika gaya musu cewa ya faru da ke, dan a yadda na fahimta basu yarda da labarin ba nima kuma har yau labarin bai kwanta min a rai ba. Amma kuma na kasa ganin laifinki ballantana in zauna inyi miki fada ko inji na tsane ki ko inji ina kyamar ki. Hakan kuma yana da alaƙa da mahaifiyar ki. Allah ne shaida ta har ta rasu ina yi mata kallon yaruwa ta, in fact zan iya kiranta da role model dina dan nakan kwaikwaye ta akan abubuwa da yawa musamman harkar kula da miji da kuma nuna soyayya ga yaya. Ina iya tuno da sanda ta haife ki Safiyya, ina tuno irin tarin soyayyar ki da na gani a idonta a lokacin da naje yi mata barkan haihuwar ki. Ban yi mamakin yawan soyayyar ba saboda la'akari da nayi da jimawar da tayi tana neman haihuwa kafin ta same ki, na kuma kara fahimtar soyayyar sanda ta gaya min cewa likitoci sun tabbatar mata da cewa bayan ke ba zata sake haihuwa ba". Na saka hannu na goge hawayen da already ya fara bin fuskata, ta cigaba "ina kuma iya tuno lokacin rasuwar ta Safiyya, a gaba na aka yi mata sutura. Abinda nafi iya tunawa a lokacin shine sautin kukan ki. You were barely two years old. Kowa a gidan yayi kokarin ya rarrashe ki amma kina ta kuka kina kiran sunan da kike gaya mata 'ammi', abinda yafi tayar min da hankali a lokacin shine idan na kalle ta a kwance babu rai kuma na tuno da cewa ruhinta yana gurin kuma tana jin kukan ki amma bata da damar rarrashin ki duk kuwa da irin tarin soyayyar da take yi miki. It broke everyone's heart, musamman saboda yadda mutuwar tata ta kasance". Ta dakata tana kokarin daidaita muryarta, daga alama kuka ne yake kokarin kwace mata. Ta cigaba "wannan shine nightmare din kowacce uwa, and I couldn't help but think about dan karamin dana Abdul Hakim, na lissafa idan nice na mutu what will happened to him? Nayi kuma tunanin taki rayuwar ya zata kasance? Tun a lokacin na fahimci kina cikin jarabawa babba kuma kin rasa wani bangare na rayuwar ki da ba za'a iya replacing ba, amma kuma ban dauka gibin da aka samu zai kai ki ga matsayin da kike ciki a yanzu ba. I offered to take you, dan inyi kokarin cike wannan gibin, bayan ni mutane da yawa sunyi kokarin daukan ki amma babanki ya hana, yaki bawa kowa ke yace shi zai raini abarsa da kansa. Ina iya tuna wata rana da muka je tare da mai gidan nan dan mu duba halin da kuke ciki, muka tarar da shi ya goya ki da zani a bayansa kina tayi masa rigima, duk da ma'aikatan da suke gidan ku amma ba zai iya bawa kowa ke ba saboda girman soyayyar da yake yi miki". Ta sake yin shiru. Muka yi shiru baki daya sai sautin kuka na kadan kadan, ta cigaba "ban sani ba ko ma'anar labarin nan da nake baki tana fitowa, ban sani ba ko kina gane me nake nufi. But you are so precious Safiyya. You are far greater than yadda kika mayar da kanki. And you have enemies everywhere. Labaran da Sa'adatu ta bani akanki, ban san wanne ne gaskiya wannan ne akasin hakan ba. Ba zan kuma yi claiming nasan abinda yake zuciyar mutane ba. Ta gaya min cewa za'a hada auren ku ke da Mustapha idan kin haihu. Amma kuma mai gidan nan shima ya gaya min cewa suna son idan kun amince zasu hada auren ku ke da Abdul. Ban san wanne ne gaskiya ba. Amma ina son gaya miki har yanzu a raina ina da niyyar daukan ki in rike ki in dai har zan samu wannan damar. In kin zabi Abdul zan so hakan. In baki zabe shi ba kuma ina so ki san cewa I will be here for you whenever you need a mother". ****. ****. ****. ****. Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you…. Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah. [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* Daga marubuciyar: Maimoon A'isha Humaira Diyam Tagwaye Jidda And now..... Safiyya *Episode Seven: The Good and the Bad Choices* A ranar ban je asibiti ba sai dare, na zauna a daki ni kadai with my thoughts thinking in nayi spending a day with my self zan iya yanke wa rayuwata shawara. Amma sai dai har daren ban zamu na yanke din ba, sai dai kamar kullum, ranar ma nayi adduoi sosai akan Allah ya dube ni ya kawo haske a rayuwata. A ranar ne kuma na fahimci dalilin da yasa na kasa samun zabi a cikin samarin da Daddy ya lissafa min, dalilin kuwa shine Gidado. In dai har zan cigaba da yiwa aure hangen da muka yi masa ni da Gidado to kuwa sai dai in Daddy yayi zuciya ya zabar min da kansa dan ba zan iya zabar kowa ba. Amma kuma sai naji cewa ina ma dai zaiyi hakan? Da ya dauke min wani babban nauyi a kaina, da ya cire min guilty feeling da nake ji a raina a duk lokacin da nayi tunanin zabar wani ba a matsayin miji wanda ba Gidado ba. In dai har ba Mustapha zai zabar min ba to bani da matsala. Abdul na san idan na zabe shi bani da matsala da iyayen sa, dan maganar da Aunty Hajjo tayi min yau ta kuma tabbatar min da kaunar da take yi min, sannan Uncle Sufyan kuma zan iya kiran shi da second father dina dan duk duniya Daddy bashi da aminin da ya amince wa kamarsa. Amma kuma Abdul yana da wadda yake so kamar yadda ya gaya min baki da baki. Kuma experience dina da soyayya ya saka na fahimci cewa kowace ce ma yana kaunar ta sosai. Duk sanda nayi tunanin zabarta sai in hasaso cewa Muhammad ne sanda muke tare muke tsara rayuwar mu tare sai iyayensa su haɗa shi aure da wata saboda selfish reason ɗin su. It would have destroyed our lives. And I do not want to destroy someone else's life dan ni in samu farin ciki. Mukhtar on the other hand yana so na, dan yana daga cikin few mazan da suka taba physically confessing soyayyar su gare ni. Mukhtar ya jima yana so na, soyayyar da ni a gurina na fara daukan ta obsession har ta fara irritating dina kuma tasa yayi loosing girmansa na yaya na a idona. In na aure shi at least zan zauna da wanda yake sona ko da kuwa ni bana son nasa amma kuma iyayensa fa? Uncle Ahmad shine dan uwa daya tilo da Daddy yake dashi a duniya, komai namu a hannunsa yake tunda Daddy ya fara rashin lafiya more than five years ago, sai dai kuma tun ina karama nake samun problem dashi da matarsa dan suna min kallon spoilt girl da bata da tarbiyya, problem din namu kuma ya karu a shekarun bayan nan, sannan ya zama worst bayan bayyanar ciki na. Zasu karbi aure na dole, and zasu iya farinciki ma da hakan, sai dai hakan baya nufin zamu daidaita dasu ko kuma zasu kasa goranta min ko nan gaba. And Mustapha, in na zabi Mustapha rayuwa ta will be a disaster, dan ban taba tsanar mutum ba kamar yadda na tsane shi and there is no way da zan iya neman aljanna ta a karkashin sa. Sai dai kuma Mommy tayi min dukkan halaccin da mutun yake nema daga wani mutum, ba ita bama, danginta sunyi wa Ammi na halaccin da duk mutum yake bukata daga mutum, musamman wanda ba dan uwansa ba. Duk da dai nasan a yanzu ba wai dan soyayya ko halacci ne yasa suke son hadin auren mu ba, but I do not care about that, da ace zan iya 'managing' zama da Mustapha, da tabbas shi zan zaba. Kamar kullum tunda muka zo garin, sai na samu kaina da yin adduoin istikhara da neman Allah ya bayyana min zabin sa a fili ya kuma tsayar min da zuciya ta akan zabin nasa. Kwana biyu bayan nan, da dare ina kwance kamar kullum ina kallon ceiling na kasa bacci, a lokacin babu abinda nake nema irin abinda zaiyi taking ɗina away from my thoughts. Na tuno da twins sai naji guilty feeling dan tun da muka rabu a Nigeria bamu sake yin magana ba. Na dauko wayata na kunna ina lissafin time ɗin Nigeria amma sai na lura dare yayi sosai a can, maybe ma sunyi bacci. Amma sai nayi tunanin hawa online in duba su. Sai dai ina kunna data din wata ta naji gaba na ya fadi, sai a lokacin na tuna cewa banyi blocking Gidado from Whatsapp ba kuma na tabbatar ya neme ni ta can. Na bude Whatsapp din na tsaya ina kallon yadda messages din suke shigowa a guje, har suka gama suka tsaya. And like I  expected, akwai da yawa daga Muhammad. Na kasa bude sakon nasa saboda tsoron abinda zan gani, zuciya ta ba zata iya daukan wasu karin bakaken maganganu daga gare shi ba. Idan kuma rokona yake ba zata iya jure cigaba da butulce wa soyayyar sa ba. Sai dai kuma a lokacin na sani har cikin zuciya ta cewa rabuwa da shi shine abu mafi alkhairi da zan yi masa a rayuwa. I couldn't stain his clean life with my dirty and tragic life. Idan ma gaya masa gaskiyar abinda ya faru da ni ba zai taɓa rabuwa da ni ba, iyayensa kuma ba zasu taɓa amincewa ya aure ni ba, nawa iyayen kuma zasu kama shi da zargin yana da hannu a cikin abinda ya sameni. So in whatever way shine a ruwa. And I rather drown myself then get him wet. Wannan shine zurfin soyayyar da nake yi masa. Message dinsa na karshe kawai na karanta. "please Piya, I just want to know why". Na rufe ido na ina jin damshin hawaye na a akan kuncina na danne conversation din mu sannan na danna delete, knowing fully well that nayi deleting dukkan chats dina da shi. Sai da nayi deleting dan kar in karanta sannan na bude nayi masa reply, duk da ban san complete abin da yace ba. Na gama rubutawa na tura masa sannan nayi blocking dinsa from my Whatsapp chats. Na saka hannu na biyu na rufe fuska ta, nayi kuka na mai isa ta sannan na bude fuskar na goge hawaye na na cigaba da scrolling through the chats ko zan samu abinda zai dan kwantar min da hankali na ko yayane. A lokacin nayi karo da messages din Yaya Mukhtar. Na bude, duk kuwa da cewa a raina na san shima wani karin bakin cikin zai kara saka wa zuciyata. Maybe ma gorin cikin jikina zai yi min. Amma kuma sai na tarar hakuri yake bani "Fiyya ban san da wanne kalaman zanyi amfani ba in baki hakuri, daga ni har Abba na san mun bata miki, a lokacin da ya kamata mu zama mune masu share miki hawaye sai kuma muka zama mune masu saka ki kuka" "Kin san halin Abba, it was just his temper talking not him, and he loves you shi yasa yake takaicin halin da kike ciki. Please kiyi hakuri ki yafe masa" "And ni kuma. You of all people know what my problem is, kishi ne yake damuna ba wani abu ba. I know I shouldn't have said zan taimaka miki in aure ki because like you said, ni ne nake neman taimako a wajen ki, cos nine nake tsananin son ki. And it would be my pleasure to marry you ko da kuwa nakasa ce ta same ki. And whatever kika haifa, zai zama ɗan mu ne ni da ke babu wanda zai san abinda ya faru. This I promise you with my life" "Please Safiyya in kinga messages ɗina ki kira ni. Ko ki kira Abba if you are still angry with me. We are worried about you. Bama samunki a waya and Daddy baya daukan kiran mu daga ni har Abba". And the last message "Ki gaya wa Mustapha, duk sanda ya shigo Nigeria sai yayi regretting. Na rantse sai na chanja masa kamanni". Na ajjiye wayar tare da yin ajjiyar zuciya. Na rufe ido na ina jujjuya kalaman Mukhtar a raina sannan kuma ina tunanin abinda ya haɗa shi da Mustapha. Dama can basu fiya jituwa ba tun muna yara. Shi Mukhtar muguwar zuciya ce da shi irin ta Daddy da Abba, shi kuma Mustapha silent killer ne, da wahala kaga bacin ransa. Ga ladabi da biyayya a gurin manya. Da haka ya siye zuciyar Daddy. But only I know who he really is. Da safe na tashi nayi wanka ina shiryawa kenan yayin da Mommy ita kuma ta shiga wanka, sai naji wayata tana kara, sai dana dan tsorata dan na manta da cewa na kunna ta. Sai kuma na fara murna ina saka ran twins ne suka kira ni, amma dana dauki wayar sai naga Uncle Ahmad ne. Nayi ajjiyar zuciya na zauna a bakin gado sannan na dauka tare da sallama. "Abba ina kwana" Ya amsa "lafiya lau Safiyya. Tunda kuka tafi sai yau kika kunna waya ne?" Nace "jiya da dare na kunna" yace "saboda menene? Saboda kima ganin babu wanda ya damu da ke da zai neme ki a waya? Ke kin kashe waya shi kuma Yaya na kira wayarsa yafi sau cikin charbi amma ba'a barinsa ya dauka. Na san kuma matar sa tare da wannan tsinannen yaron Mustapha. Har Mustapha ne ni zan kira Yaya ya dauka yace min wai bacci yake yi yace kar a dame shi. Ni fa?" Na dafe kaina saboda already har naji ya fara yi min ciwo da safiyar nan. Nace "kayi hakuri Abba, in sha Allah yau in naje asibitin sai in kira ka in bashi wayar kuyi magana" Ya danyi shiru "eh ina son magana dashi sosai, ke ma kuma ina son magana da ke. Ina son in baki hakuri akan abinda ya faru ranar nan. Na fahimci shine dalilin da yasa Yaya yake fushi da ni. Ni ba dan wani abu nayi miki fada ba sai dan ina ganin na isa inyi miki fadan ne. Uwa daya uba daya ne suka haife mu ni da Adam. Ke a matsayin ƴa kike a waje na. Ban dauka dan nayi miki fada Yaya zai dauki fushi dani har ya daina yi min magana ba. Ban dauka dan nayi miki fada zaki je ki kai kara ta gurin sa ba". Na girgiza kai kamar yana kallona nace "Abba wallahi ban kai karar ka ba. Ba da niyyar kai karar ka nayi masa magana ba....." Ya katse ni "I know Safiyya. I understand. Wannan matar tasa ce zata hada. She have brainwashed you two ba kwajin maganar kowa sai tata. Ba kwa daukan kowa da mutunci sai ita da yayanta. Ni na san ita ce ta saka ki kike ta bina akan wai sai na dauki kuɗin ki na siya wa ƴaƴan ta motoci " na sake girgiza kaina "Uncle ba ita ta fada min ba, ni ce .." yace "ba zaki gane ba Safiyya. Ba zaki gane ba. Kamar yadda nace, she have brainwashed you". Nayi shiru ban ce komai ba a lokacin da Mommy ta fito daga toilet tana kokarin shiryawa. Yace "in kinje asibitin ki gwada hada ni da Yaya ko Allah zai sa ya sauko muyi magana. I am not feeling comfortable with you two tare da su. Hankali na ba'a kwance yake ba" na gyada kai ina kallon Mommy da ta tsaya da abinda take yi tana kallona. Nace "insha Allah, zan yi masa magana in naje. Insha Allah, komai zai dawo dai dai" yace "good. Idan kinyi haka kin kyauta mana gabakidaya. Dan duk duniya baku da wadanda suka fi mu. Muma kuma duk duniya bamu da wanda wadanda suka fi ku". Na cure wayar daga kunne na na ajiye ta a gefe, Mommy da har lokacin take kallo na tace "waye?" Nace "Uncle Ahmad ne " ta bata rai "Ahmad ba shi da kunya wallahi. Me kuma yake ce miki bayan irin wulakancin da yayi miki a cikin mutane? Me kuma zai ce miki?" Nayi shiru da farko, amma ganin alamar amsa take jira sai nace "yana so yayi magana da Daddy ne. Yace baya samun sa a waya" tayi tsaki, "to ba dole yaki daukar wayarsa ba. Ta yaya za'a yi mutum ya cire maka zani a kasuwa sannan kuma yazo gida yace zai daura maka? Na dauka ma maganar wannan marar kunyar yaron zai yi miki. Wannan yaron ko maye ne shi to sai dai yaci kansa wallahi dan kin fi karfin sa". Haka ta cigaba da maganganun ta ni dai har na gama cin abinci na na kammala shiryawa ta. Sannan ita na taci muka fito muka yi wa Aunty Hajjo sallama muka tafi. Tun a mota ta bawa Mustapha labarin nayi waya sa Uncle Ahmad, ina jinsa yana bata hakuri wai kar ta sawa kanta damuwa shine maganin daga Uncle Ahmad ɗin har Mukhtar. Ni dai bance musu komai ba duk kuwa da kokarin saka ni da suke yi a cikin maganar. Muna zuwa asibitin muka tarar an yi discharging Daddy. Sun gama bashi duk wani treatment ɗin da zasu bashi babu kuma sauran wani abu da zasu iya yi masa. Wannan shine dama mostly abinda ake yi masa a duk asibitocin da muke zuwa. Sai dai suke mana muje gida in wani symptom din ya sake bayyana ko wani ya zama worst sai mu dawo. Amma cutar sa babu magani. Har yanzu ba'a samu maganin ta ba. Sai a lokacin nake jin ashe Daddy ya saka an kama mana apartment din da zamu zauna kafin sanda za'a yi min aiki. Plan dinsa dama shine in an sallame shi mu samu gida mu zauna baki daya har sai na rabu da cikin jikina sannan zamu koma Nigeria. Damuwarsa kuma har lokacin ita ce bai san yadda zaiyi da abinda za a ciro daga cikin nawa ba and definitely baya son mu zauna tare da abinda zan haifa. Bai san already na samo solution to that ba. Sai da na bari ya tura Mustapha ya karbo sauran magungunan da akayi masa prescribing, Mommy kuma ta fita gurin nurses zata yi making some inquiries sannan na jawo kujera kusa da shi kaina a kasa nace "Daddy, Uncle Ahmad yace yana ta neman ka a waya baya samun ka". Ya bata rai "ina ganin kiran nasa ai. Me zai ce min? Ban dauka yana daga cikin wadanda zasu goranta min a duniya idan wata kaddara ta fada min ba". Na girgiza kaina "ba gori yayi min ba Daddy. Faɗa yayi min" ya dauke kansa yace "haka yace miki kenan? Da ke yake so yayi amfani ya dawo gare ni kenan. Na riga na yanke hukunci, in Allah ya sauke ki lafiya mun koma Nigeria zan karbe komai namu da yake hannunsa. In kinyi aure lokacin your husband can take care of everything for us" naji hawaye yana taruwa a ido na. Na sake cewa "Daddy, duk duniya fa bamu da wanda ya fishi. Blood is thicker than water" yayi dan karamin murmushi "haka yace miki?" Na sunkuyar da kaina ina wasa da yatsuna ban ce komai ba. A lokacin na kammala yanke hukunci na. Na dago kai nace "Daddy na yanke shawara, akan zabin da ka bani" Ya juyo yana kallona amma bai ce komai ba. Nace "na zaɓi Mukhtar. Mukhtar zan aura". ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.     A bangaren Gidado ya dan samu sauki, ba wai saukin zafin da zuciyarsa take yi masa ba sai dai yanzu iyayensa sun dan sauko duk da dai basu dawo yadda suke da ba. Still suna blaming dinsa for being negligent, for being vulnerable, for letting a small girl toyed with his emotions. Two days after zaman da suka yi dashi ne suka sake kiran sa suka gaya masa hukuncin da suka yanke a kansa. "Ba za'a fasa haɗa bikin ka da na Mufida ba kamar yadda muka yi niyya. You are going to get married" Ya dago kai yana kallon su, feeling confused. Abba yace "ka duba cikin yan'uwa, tun daga yalleman zuwa Kano zuwa Abuja, ka fitar da mata, cos you are getting married in the next two months". Ya juya yana kallon Mama, hoping ko zai samu wani hope daga gare ta, amma sai ya ga taki yarda su haɗa ido kuma a duk sanin da yayi wa iyayensa duk maganar da daya yayi to dayan ma ita yake goyon baya. Abba ya cigaba da magana "believe us Muhammad, it is going to be the best thing that has ever happened to you. Duk kan mu mun san bayan abinda yarinyar can tayi maka, it will take time for you to heal and trust women again, and from our experience, the best feeling ever is to fall in love after marriage. And it is the most easiest. To make things easier for you, mun baka zabi. Choose wadda duk kake ganin zaka iya so later on, mu kuma zamu yi wa iyayen ta magana and if bata da wanda take so, shikenan" Gidado ya sake juyawa ya kalli Mama, ta fahimci yana bukatar ta, tayi ajjiyar zuciya tace "It is going to be okay Gidado. Wannan shine decision ɗin mu. Kuma sai da mukayi dogon tunani kafin mu yanke shi. And ba zamu taɓa yin abinda zai cutar da kai ba. Kuma in kayi biyayya a gare mu ba zaka taba nadama ba" Ya sunkuyar da kansa kasa a zuciyarsa yana hoping ina ma dai shi mace ne, ina ma dai zai iya zama yanzu a gaban iyayensa yayi ta rusa kuka har sai sunce sun janye hukuncin da suka yanke. Jin yayi shiru ya saka Mama ta sake cewa "ina fatan yarinyar nan bata saka dafinta a zuciyar ka har level ɗin da zai kai ka ga bujirewa maganar mu ba". Ya dago kai yana jin zazzaɓi yana neman rufe shi yace "ɗan Allah Abba, ina neman alfarmar a bani lokaci in yi...." Mama tace "dawa zaka yi shawarar? Da ita?" Ya girgiza kai da sauri "ba da kowa zanyi shawara ba Mama. Zan dan tattauna maganar ne da zuciya ta. I just want to have some time to think " Mama ta sake cewa "babu komai a zuciyar ka Muhammad sai soyayyar waccan matar. I have seen the kind of messages da kake tura mata. I have read yadda kake begging dinta kamar wadda take rike da ranka a hannunta" ta karasa maganar cikin dacin murya and he can literally feel irin tsanar da take yi wa Safiyya. Abba yace "tomorrow. You have until tomorrow". Ya maimaita "tomorrow. Okay" sai kuma ya mike da sauri ya fita waje. Sai da yaje wajen sannan ya tuna babu abinda zaiyi a wajen. Babu gurin wanda zai je wanda zai iya hana iyayensa abinda suka yi niyyar yi. His grandparents will definitely back his parents up musamman in suka ji abinda ya faru, his auntie and uncles too, and then marriage proposals will start flying from alla angles. Babu irin tunanin da bai zo kansa ba. If only he can see Piya maybe he can convince her leave her husband tazo su yiwa iyayensa karyar cewa maganar da ma ba haka bace ba misunderstanding aka samu, and then get married. Sai kuma ya dafe kansa yana tunanin ta yadda aka yi ma har yayi irin wannan tunanin. Lallai soyayya babu abinda bata sakawa dan a lokacin abubuwa kadan ne ba zai iya aikatawa ba dan ya samu Safiyya. Love yana kokarin turning the good boy he is into a bad boy. Ya dauko wayarsa and for the nth time ya kira number ɗin Safiyya. "Common Piya" ya fada yana jin ransa yana kara baci. How can you love and hate someone so fiercely at the same time? Ya buɗe motarsa ya shiga, ya kalli side ɗin da take zama hoping to see her appear ko da na second daya ne. Sai kuma ya dauke kansa ya tayar da motar ya fita daga gidan a guje. Sai dai kuma shi kansa bai san inda zaije ba. Bai san abinda zaiyi ba. MD University ya dosa, the first time da ya shiga tun ranar da suka rabu da Safiyya. Kamar yadda yayi tsammani babu mutane sosai a cikin makarantar saboda dalibai suna hutu, but yana hoping wanda yaje nema yana nan. Ko baya nan ma zai nemo shi duk inda yake. File din Safiyya yake so a dauko masa, address din ta yake so a bashi, kano zai je a yau yaga babanta or her husband, whatever the case maybe. In yaje sai ayi duk wacce za'a yi. Ya dauko wayarsa da niyyar kiran wanda zai karbi informations din a hannun sa, sai dai garin neman number ɗin ya lura da notification din da ya shigo masa wanda bai ma lura da sanda ya shigo ba. A message from Piya 💝. Wani faduwar gaba yaji, and then cikin rawar hannu ya bude message ɗin ya karanta. "Dear Muhammad. I am very sorry for what happened. Please find it in your heart to forgive me ko ba yanzu ba. But for now, please stop trying to contact me. And don't look for me dan Allah. I have made a mistake naci amanar mijina with you. Now I have repented bana son in kara aikata kuskuren da na aikata a baya". "Mijina bai san abinda nayi ba and I want to keep it that way. Bana son in breaking heart dinsa because I love him so much. Please, do not break up ny happy home. You will soon get over me and move on as I have gotten over you". "Dan Allah, for the sake of the love that you have for me. Don't let my husband know". Ya maimaita jaranta message din ya kai sau uku, sai ya rufe shi ya sake budewa hoping it will disappear amma still yana nan. Wayar ta zame daga hannun sa ta fada kan kafarsa, yayinda shi kuma ya saka hannu biyu ya rungume kirjinsa dan ji yake yi kamar zuciyar sa zata fito. Sai kuma ya kifa kansa akan stirring motar. Ya jima a haka kafin da dago, ya kunna motar ya jata a guje ya fita kamar yadda ya shigo a guje. Ya jima yana zagaya gari ba tare da yasan inda zashi ba, har sai da yaga rana tana neman faduwa sannan ya doshi gida, zuwa lokacin already ya yanke decision ɗin sa. Yana shiga gida ya samu Mama a zaune a falo suna hira da Mufida. Suka bishi da kallon mamaki da kuma tausayin yanayin sa. Ya zauna daga can gefe sannan yace "Mama na yanke shawara akan maganar da kuka yi min dazu" ta gyara zama tana kallon sa tace "ba sai gobe ba?" Yace "babu bukatar hakan. Babu bukatar jiran gobe. Babu abinda zan chanja tsakanin yau da gobe. Na amince da maganar auren da kuka yi. Allah ya sa albarka. Amma ina neman alfarma guda uku. Na farko ina so ku zaba min da kanku, bana jin zan iya zaba da kaina. Na biyu ina son dan Allah duk wadda zaku zaba ya zamanto ta amince da kanta ba takura mata aka yi ba, zan so kuma ace tana sona ne dama, at least that will make things easier. Na uku, Please, kar ku zaba daga cikin yan'uwa, nafi son bare". Mama ta bata rai tace "why not? Me yasa bayan muna da yammata masu hankali da tarbiyya da ilimi, wadanda kuma muka yarda da su muka yarda da asalin su sai mu tsallake su mu tafi nema a wani wajen? Ta yaya gida bai koshi ba zamu bawa daji?" Ya girgiza kai "Mama, there is a chance that this may not work. And I value zumuncin mu da yan'uwan mu a lot that bana son in zama sanadin samun sabani tsakanin mu. Please ku nema min bare yadda ko ba'a dace ba effects din ba zai zama da illa sosai ba". Mama tace "to ni yanzu Muhammad ta ina zan fara nema maka mata a cikin dan lokacin da muke da shi. Yaushe aka samu matar har aka yi neman auren da bincike da komai?" Mufida da take kwance tana jin su ta mike zaune tace "Mama in kin yarda akwai friends ɗina. Akwai wallahi da yawa da sun sha yi min maganar suna son sa ni kuma ban taba yi mishi magana ba saboda nasan ba kula su zai yi ba. Idan kin yarda sai in bashi pictures din su ya zaba, duk yayan manyan mutane ne, babu kuma wacce iyayen ta ba zasu iya aurar da ita a cikin wata biyu ba" Ya sake cewa yana kallon Mufida"I don't want to choose" shi a cikin zuciyar sa gani yake yi kamar idan ya zaba yace ya zabi wance kamar yaci amanar Safiyya ne. Mama ta kalle shi kawai tayi ajjiyar zuciya, bata jin zata daina tsinewa yarinyar nan. Mufida ta sake cewa "to bara in nuna wa Mama ta zaba maka ita, ta san most of them already, har iyayen su ma ta sani" ta fada tana dauko wayarta. Sai kuma ta tsaya kamar wadda ta tuno wani abu tace "oh my God. Oh my God" Mama da Gidado duk suka juyo suna kallon ta. Gidado ya juya mata hannu alamar tambaya, ta koma ta zauna sosai tace "akwai wata yarinya, kusan shekara guda kenan tana yi min naci akan in haɗa ta da kai" ya bata rai yace "wacece?" Tace "I don't know her. Kawai a one of the northern blogs na Instagram naga ta tura irin hide my ID post din nan da hoton ka, wai tana cigiyar ka ko kuma wanda ya sanka, wai tana son ka. I commented cewa kai yayana ne amma already kana da wadda kake so. She followed me into my DM tana ta yi min nacin in bata ko da number din ka ne ta gwada sa'ar ta, na gaya mata ba zaka kula ta ba taki yarda, I gave her your number dan ta tabbatar da kanta. She later told me ta kira ka baka dauka ba, she sent you a message kace mata tayi hakuri kana da wacce kake so and you blocked her " Gidado yayi shiru yana tunani, ba zai iya gane wacece ba because a lot of that scenario has happened, yammata da yawa sukan gwada sa'ar su a kansa and all the times ya kan basu hakuri and then blocked them dan baya son ciwon kai. Mufida ta cigaba "tun lokacin bata hakura ba. Har daina daukan wayarta nayi na kuma daina replying messages dinta amma bata daina kira na da kuma turo min sako ba. She even sent me some of her pictures wai in nuna maka. And she is beautiful gaskiya. Daga alama kuma yar manyan mutane ne ce. Let me see it I still have the pictures" ta fada tana bude wayarta Gidado ya mike tsaye "unknown girl. With no link or connection to the family. She is perfect. Call her and ask her if she is still interested. And if she can get married in the next two months. Then get her information. Duk abinda ta gaya miki sai ki gaya wa Mama" ya juya ya fara tafiya zuwa bangaren sa. Mama ta daga murya tace "haka kawai kake tunanin zamu aura maka yarinyar da ba'a san asalin ta ba, daga haduwa a social media?" Ya juyo yace "in akayi bincike za'a samo asalin ta. In asalin baiyi muku ba sai Mufida ta samo wata unknown din" Yana jin ta tana cigaba da magana amma baya fahimtar me take cewa. Tafiya kawai yake yi yana jin zuciyarsa tana breaking into thousand pieces. ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    Assalamu alaikum masoya littatafan maman Maama, babu abinda zan ce muku sai godiya sai kuma ban hakuri. I have not been doing well with posting Safiyya na sani, and it has gotten worst. A yanzu haka kuma dole in sake baku hakuri dan zan ɗan dakata da rubutun Safiyya saboda abubuwa da yawa da suka sha kaina wadanda ba yadda zan yi da su. Kuyi hakuri, kuyi hakuri, kuyi hakuri.... Dani da Safiyya da Gidado muna baku hakuri. We will resume insha Allah as soon as nayi clearing issues ɗin da suke gaba na. Please ku taya ni addu'a, I really need it because I am faced with one of the toughest challenges dana taba fuskanta so far. Allah ya bani sa'ar abinda yake gaba na a yanzu. We will see the end of Safiyya together insha Allah. Wadanda suka fara biyan sponsorship in suna sauri ne suyi min magana for a refund. Nagode. Ma'assalam [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹Safiyya❤‍🩹* *By* *Maman Maama* *Episode Eight: The Acceptance* Free Episode *Her🧕🏻* Ya dago kai yana kallona da fuskar mamaki, nayi sauri na mayar da nawa idanuwan kasa tare da rike numfashi na dan na san abinda zai biyo baya "Mukhtar?" Ya tambaya cikin mamaki "Mukhtar fa kika ce? Are they blackmailing you? Cewa suka yi in baki aure shi ba zasu gaya wa duniya abinda kika aikata?" Na fara girgiza kaina amma ban ce komai ba, na fahimci dama tunda yana jin zafin uncle Ahmad dole zaiyi retaliating akan zabin nawa duk kuwa da cewa shi ne da kansa ya lissafa min har da Mukhtar din a cikin options dina. Amma ban dauka zai dauki zafi haka ba. Cikin fada ya sake tambaya ta "baki bani amsa ba, are they threatening you?" Mommy ta shigo da takardu a hannun ta, ta tsaya tana kallon sa sannan ta kalle ni cikin alamar tambaya, ban ce komai ba ta mayar da tambayar ta kansa. Cikin dacin rai ya nuna ni yace "wai Mukhtar. Wai Mukhtar zata aura" Ta zame ta zauna akan kujera tana dafe kirjin ta "na shiga uku ni Sa'adatu. I thought you hated that guy. You said it yourself several times." A hankali nace "I never hate him, he is my cousin. I just don't love him. Kuma har yanzu bana son sa. Bana masa soyayya irin ta aure amma duk kunsan cewa shi yana so na and at least that is something". Mommy ta nuna waje da hannun ta "and so does Mustapha. In dai soyayya ce Mustapha yafi Mukhtar son ki. Yafi su son mahaifin ki da yanuwanki. Yafi kowa dace wa da auren ki. Da kika ce ba zaki aure shi ba na dauka Abdul zaki aura knowing fully well cewa ba kya son auren Mukhtar. Ashe zaki iya zaben wanda kika ambata xewa ba kya so akan Mustapha? Gwara kikai kanki inda na tabbatar ba son Allah da Annabi suke miki ba akan ki zauna a inda za'a fi ko ina mutunta ki?.........." Ta cigaba da fada muryarta har shakewa take yi yayin da ni kuma na saka hannayena biyu na toshe kunnuwana tare da rintse ido na. Da bi ar da nake yi a duk sanda ake kokarin chanja min ra'ayi akan abinda na riga na yanke shawara akan sa. Sai da naji na daina jin muryarta sannan na dube ido na ina kallon Daddy shima yana kallo na idonsa cike da mixed emotions. "Wani abun Ahmad ya gaya miki a waya sanda ya kira ki wanda ya saka kika yanke wannan hukuncin?" Ya tambaya muryarsa da sanyi akan dazu. Na girgiza kaina tare da goge hawayen da bansan sanda na fara zubar da su ba nace "bani da wani zabin ne Daddy. Ba zan iya auren Mustapha ba. Abdul baya sona. Bazan iya auren wanda nake so ba. Bani da zabi Daddy" ya gyara zamansa "waye wanda kike so ɗin? Ki gaya min waye shi ni kuma zan aura miki shi in dai har na bincike shi naga ya chanchanta. Zan aura masa ke kuma in mayar masa da ɗan shi. Waye shi?" Na mike tsaye "ba ɗan shi bane ba Daddy. Ba ɗan shi bane ba. Ban san waye uban ɗan ciki na ba amma ba nashi bane ba. Ba zan makala masa laifin da nake da tabbas ɗin ba shi ya aikata ba. Ba zan bata tsakanin sa da iyayensa in kuma bata masa suna a gari ba" Ya dafa kujera ya mike shima, bacin rai yana sake dawowa fuskarsa "kina da shaidar cewa ba shi bane ba kenan? In har ba ki san waye ba zai iya zama shi ɗin ne kenan. Wato da ki bata tsakanin sa da iyayensa gwara ke kin bata da naki iyayen ko? Da ki bata masa suna gwara kin bata naki sunan kin zauna da tabo na har abada a tare da ke, gwara kin auri wanda ba kya so wanda shima kuma ba son Allah da Annabi yake yi miki ba, gwara kin zauna da ɗan da in ya girma ya tambaye ki waye ubansa baki da amsar da zaki bashi ko? Gwara kinyi watsi tare da fatali da duk sacrifices da mahaifiyar ki tayi domin ki, domin ki samu kyakkyawar rayuwa ko? She gave you everything, she gave her very life for you". Ya karasa cikin daga murya. Nace "but I never ask for it. I never ask for any of this. I wish she didn't do what she did. I wish she let me die" Na juya da sauri na fita daga dakin ina kuka, ina jiyo muryar sa yana kwalla min kira "Safiyya, come back here" ban waiga ba ballantana in koma. A waje na samu kujera na zauna na kife kaina ina cigaba da rusa kuka na. Har cikin zuciya ta a lokacin fata nake ina ma dai Ammi bata yi duk abinda tayi ba. Da yanzu ban samu kaina a cikin wannan matsalar ba dan ko shakka babu abinda tayi din shine silar shiga ta halin da nake ciki. Ina cikin kukan naji an zauna a kusa da ni. Ban dago kai ba thinking wani stranger din ne. Sai da naji an ambaci sunana "Fiyya?" Na dago kai da sauri na kalli side ɗin, duk da kuwa na gane muryar wanda yayi min maganar tun kafin in kalle shi. "Fiyya what happened. Me ya saka ki kuka har haka?" Na saka hannu biyu ina goge fuskata duk kuwa da cewa ba tsayawa hawayen suke yi ba. "Fada muka yi da Daddy " na fada cikin sheshshekar kuka. Ya gyada kai "yes. Ina tsaye ai kika wuce ni baki ganni ba. Amma Fiyya mai zai kai ki fada da Daddy a halin da yake ciki? A halin da kike ciki? Me ya haɗa ku" ya fada yana miko min hanky. Na karba tare da kokarin tsayar da kuka na. Ya sake cewa "talk to me.... At least let it out of your chest " na girgiza kaina "ba zaka gane ba Abdul" ya gyara zaman sa "Try me. Wata kila zan gane har ma in baki shawara. And just so you know, Mama ta faɗa min komai a kanki. She told me about your situation. She said she wants me to marry you" na juyo ina kallon sa na fahimci da gaske yake abinda ya fada, but I still noticed the sadness in his eyes. Na danyi murmushin tausayin rayuwata nace "Allah sarki Aunty Hajjo. Lallai ta cika kawai kwarai. Ammi would be very proud of her" yayi ajjiyar zuciya "yeah. I guess so" nace "but I will not marry you Abdul" ya jiyo da mamaki, nace "na riga na yanke shawara, Mukhtar zan aura. Hakan shine sanadin fadan mu da Daddy. And I am not changing my mind. Tunda ai shi ya bani options ɗin kuma na zaba" ya danyi shiru yana tunani sannan yace "but why him? Me yasa kika zabe shi? Why not me?" Nace "I am not sure why. Kawai dai nayi addu'a and naji a raina shi ya kamata in dauka. And personally, na farko I believe yana so na da gaske. Cos ya jima yana ta bina da maganar soyayya ina ƙi, nacin da yake yi min da kuma goyan bayan sa da uncle Ahmad ya fara yi shi ya saka na bar gidan su da zama a Abuja na koma hostel. Shi kuma Daddy ya goya min baya yace ba za'a yi min dole ba. Wannan shine silar fara rikici tsakanin Daddy da uncle. And secondly, ina ganin auren mu zai gyara tsakanin Daddy da dan uwansa. He needs him a yanzu. Su biyu iyayensu suka haifa, bashi da kowa sama da shi" Abdul ya gyada kai cikin fahimta "at least in yana son ki auren will be much easier on you" na ce "yes. And kai kuma abinda yasa ban zabe ka ba shine, akwai wani wanda nake so, shine dalili na biyu da yasa muka yi faɗa da Daddy. I love him so much shima haka. So ina imagining yadda muke dashi idan da ace wannan kaddarar bata fado min ba, ace kawai a gidan su a yanke shawarar cewa ba zai aure ni ba wata yar abokin babansa wadda tayi cikin shege zai aura. It would have destroyed him and me. I don't want destroy you and your girlfriend" Yayi murmushi, I can see his love for her a idonsa, yace "thank you. I really appreciate what you did. Kin yiwa soyayya halacci. And ina ganin zabin ki shine dai dai. Amma pardon me for asking, ya labarin wancan guy din da kike so ɗin? What happened to him? Ya san halin da kike ciki?" Na yi shiru ina kallon yatsun hannuna, ban so nayi mishi magana akan Muhammad ba dan ko tunawa da Muhammad bana son zuciya ta tayi saboda irin damuwar da nake shiga idan na tuno shi, nace "I can't even imagine halin da yake ciki. Soyayya ta bata yi masa halacci ba. It destroyed him". Waya ta tayi kara. Na dauko ta daga cikin jaka ga mamaki na sai naga number ɗin Mukhtar. Na kife ta akan cinyata tare da rufe fuskata da hannayena. Na fahimci Daddy ya hakura kenan saboda fushin da yaga nayi, har ya kira uncle Ahmad ya gaya masa zabina shi kuma har ya gaya wa dan na sa. Or not. Ni na zaba da kaina amma yanzu a raina bana jin zuciya ta zata karbi zabin nawa, da zata so Mukhtar da tini ta so shi. "Ana kiran wayarki" Abdul ya fada yana kallo na. Na bude fuskata tare da daukan wayar na amsa kiran "hello?" Daga daya bangaren aka amsa "Hello Habibty" *Him👳🏻* Bai tsaya ba har saida ya shiga dakinsa sannan ya rufe kofa ya jingina bayan sa da jikin kofar tare da rufe idonsa yana jera numfashi kamar wanda yayi gudu. Sai kuma ya bude idon ya fara magana da kansa. "Yes. Wannan shawarar tayi. I will get married and I will forget about her, and fall in love with my wife and have kids like every other person. Babu wani abun da zai chanja. There is nothing special about her. She is just like every other girl". Ya kwanta akan gado ƙafafuwan sa a kasa yana kallon ceiling, a ran sa yana jera yadda zai cigaba da tsara rayuwar sa step by step. Farko, da farkon fari kafin ya fara komai zai fara da cire Safiyya daga ransa dan in dai har tana yawo a cikin zuciyarsa babu abinda zai iya aikatawa. And to forget about her sai ya fara raba kansa da duk wani abu da yake tuna masa da ita. Ya mike zaune yana karewa dakin kallo, bata taba shiga dakin na sa ba amma kusan a kowanne angle na dakin akwai memory dinta, ko dai wani abu da ta bashi ko kuma abinda suka yi maganar sa ko ta saka ya siya da kansa. Yayi tsaki tare da yanke shawarar cewa dakin zai bari gabaki daya ya koma wani. Nan da two months ma gidan zai bari gabaki daya ya koma nasa gidan shi da matarsa. Sai dai kuma shima wancan gida babu abinda babu memories din Safiyya a ciki. Ya sake yin wani tsakin. One step at a time. Dole zai manta da ita amma one step at a time, tunda dama ai ba lokaci daya ta shiga rayuwar sa tayi zurfi haka ba. Ya dauko wayarsa ya fara da step din farko. Numbers dinta ya nemo duk yayi blocking sannan yayi deleting. Sai kuma ya nemo dukkan messages dinsu da chats dinsu duk ya haɗa kansu ya goge. Ya ajiye wayar tare da rufe fuskarsa da hannayensa, a ransa yana jinjinawa kansa. "You can do it" ya fada wa kansa. Ya bude fuskar tare da sake daukan wayar yana jujjuya ta. Tare ya siya musu wayar iri daya shi da ita. Too many memories. Ko dai ya ajiye wayar kawai ya chanja wata? Amma in ya ajiye ma zuciyarsa zata iya rinjayar sa wata rana ya dauko ya kunna ya duba pictures da videos dinta da suke fal a ciki. To completely forget about her dole sai ya goge wadannan ma. Ya bude wayar da sauri ya fara nemo pictures da videos din da duk take ciki yana marking, yayi marking da yawa har yazo kan wani video da bai tabbatar nata be ko ba nata bane ba sai ya bude shi dan ya tabbatar. And then he saw her face, as clear as a lokacin ne yake daukan ta video ɗin. Kuka take yi shabe shabe da hawaye a cikin video ɗin tana bubbuga kafa a kasa irin yadda shagwababbun yara suke yi. Yana jin muryarsa a ciki yana dariya "wai da gaske kukan kike yi? La ila! Mutane fa suna kallon ki" ta turo baki tare da tabe shi, sak yar yaye, "ni wallahi ba zan daina kukan ba sai ka siya min ice cream". Ya kife screen din wayar akan gadon tare da kife fuskarsa akan wayar yana jin zuciyarsa kamar zata fado kan gadon. Ya tuna ranar da ya dauki video din. Ranar sun haɗu a school da safe tace masa mura take yi, daya tambaye ta abinda ya saka ta murar sai ta bashi labarin cewa ruwan sama aka yi da assuba ita kuma ta shiga ciki tayi wanka. A ranar da ya kira ta da dare sai yaji muryarta har ta dashe saboda mugun kamu da murar tayi mata. Babu shiri ya dauki mota ya tafi hostel ɗin su ya dauke ta da niyyar kai ta pharmacy ya siya mata maganin mura. ****. ****. ****. ****. ****. ****. A hanya ya lura da yadda take ta takurewa a cikin hijab dinta. Ya kalle ta yana lura da yadda idonta yayi ja. Yayi tsaki "pharmacy din nan ba zai yi ba Piya, asibiti zamu tafi, naga alamar ma harda zazzaɓi a jikin ki" ta bude ido tare da saurin sakin jikinta. "babu zazzaɓi fa. Allah babu. Mura ce kawai ita ma yar kadan" ta karasa maganar tare da yin atishawa. Ya harare ta "yar kadan? Wannan murar ce yar kaɗan ɗin? Asibiti zan kaiki. Let me call our doctor inji in da yake. Ya kamata a duba ki sosai" ya fada yana daukan wayarsa. Tayi saurin karbe wayar daga hannunsa. "Please kar ka kira shi. Ni na warke ma" yayi slowing down yana kare mata kallo, sai kuma yayi dariya "yanzu na gane matsalar ki. Tsoron allura kike yi" ta tura baki "babu wani tsoron allura, kawai ni lafiya ta kalau ne shi yasa" yayi kokarin juya steering motar "okay tunda ba kya tsoron allura muje asibitin kawai" ta saki wayar tare da saurin rike hannunsa "na shiga uku. Dan Allah kar ka kai ni asibiti" ya cigaba da yi mata dariya yana kallon yadda take zazzare ido kamar wadda za'a yanka "wannan tsoron asibitin naki Piya, duk ranar da zaki haihu bansan yadda za'a yi ba". Sai kuma taji kunyar sa ta rufe ido. Sun jima suna rigima a mota, daga karshe pharmacy ɗin ma cewa tayi ba zata je ba sai da kyar sannan ta yarda amma da sharadin cewa ba zata shiga ba shi kadai zai shiga ya karbo mata magani ya fito. Haka da suka je ya barta a mota ya shiga shi kadai, sai dai ga mamakin sa ya na tsaye a gurin cashier sai ganin ta yayi ta shigo gurin ta shiga bangaren da suke siyar da kayan ciye ciye, jimawa kadan sai gata da manyan robobin ice cream guda biyu, ta ajiye a gaban cashier tana kallon sa tace "one for you and one for me" ya girgiza kansa "no, no, no. Babu yadda za'a yi kina wannan murar ki sha ice cream. I won't allow it ". Ta kwabe fuska "ni Allah sai na sha. Ai naji wani doctor yace ba shan abu mai sanyi ne yake kawo mura ba, mura viral infection ce, kuma ......" Yace "oh! Viral infection? Shi yasa naga kin shiga ruwan sama kin fara mura? Ko virus ɗin a cikin ruwan saman yake?" Ya karasa maganar yana daukan robobin da niyyar mayarwa. Ta bishi da sauri "ni dai kazo ka siya min. Allah in baka siya ba ba zan fita daga shagon nan ba zama zan yi in yi ta kuka" ya juyo yana kallon ta da mamaki. "kuka? Really? To kiyi ɗin mu gani. Ni kuma I will record you and show our kids" Ai kuwa ranar yaga rigima. Tun da ya hadu da ita dama ya fahimci shagwababbiya ce amma bai san irin girman shagwabar tata ba sai ranar. A dole sai da ya sai ice cream din nan har da karin chocolates, mai shagon yana ta yi musu dariya. Suna shiga mota ta darko roba daya ta buɗe ta fara sha. Ya zauna kawai yana binta da kallo. Tayi atishawa ta kara diban wani ice cream din ta sha. Ta juyo tayi masa gwalo. Yayi ajjiyar zuciya. "This has to change. My no has to mean no and my yes yes. Dole ki ringa jin magana ta in nayi miki ita" ta juyo tare da saluting dinsa irin yadda sojoji suke yi tace "Yes Sir!". ****. ****. ****. ****. ****. *** "Hamma. Hamma Gidado. Yaya Gidado". Kamar cikin mafarki yaji muryar Mufida tana kiran sunan sa, duk kuwa da yasan cewa ba bacci yake yi ba sai dai yayi matukar nisa a cikin tunanin sa. Ya dago fuskarsa ya sauke jajayen idanun sa akan Mufida da take tsaye a bakin kofar dakinsa da waya a hannun ta. Ta dan tsorata kadan sai kuma yaga tayi sauri ta rufe mic din wayar hannunta da daya hannun, tace "uhm dama waya ce aka ce in kawo maka. Amma bara in ce mata kawai you are busy zaka kira ta an jima" ya tashi ya zauna sosai ya a shafa goshin sa yace "who is it?" Tace "yarinyar da muka yi maganar ta dazu ce. Mama tace in kira ta dan a samu information ɗin ta. Shine na kira ta ita kuma tace in kawo maka" ya sauke ajiyar zuciya, with all his heart yana son yayi rejecting kiran ya fadi wani excuse ɗin amma kuma yasan bashi da wani excuse ɗin fadi. Ya san shi yayi choosing wannan option ɗin amma accepting ɗin choice din nasa yana kokarin ya zamar masa nightmare. Ya mika mata hannu. "Give me the phone " ta bude mic din sannan ta mika masa. Yana karba ta juya ta fita. Ya zauna yana kallon timer din kiran tana cigaba da reading, sai da yayi ajjiyar zuciya sannan ya saka ta a kunnen sa, "Assalamu alaikum " yace, daga daya barin yaji ance "Ameen wa alaikumus salam Habibi" yayi shiru bai ce komai ba, sai ta sake cewa "Mufida ce ta kira ni. She told me the most wonderful news ever. Ina so ka sani cewa tunda nake a rayuwata ba'a taba gaya min labari mai daɗin wannan ba" ya sake yin shiru sai kuma ya fahimci shi take jira yayi magana sai yace "okay. I am glad you feel that way. But uhmm, this is just a procedure, I don't want to give you any false hope. Maganar aure ce and dole sai an gudanar da bincike. Am sure she told you abin yazo ne lokaci daya. I have been giving two months in fito da mata. So I am going to need some information from you and if the background check comes back okay then that's when we will celebrate" ta dan yi dariya kadan "it is going to come out okay. Everything will insha Allah be okay. And I am going to make you the happiest insha Allah. And ." Ya katse ta "Okay. Uhmm. First, menene sunan ki? Ni sunana Muhammad Lawan Muhammad. Ana ce min Gidado" tace "I know. I know a lot about you. Ni sunana Safina. Safina Ibrahim" [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹 Safiyya*❤‍🩹 By *Maman Maama* *Episode Nine: Safina* Free Episode *Him 👳🏻* "Safina?" Ya maimaita da mamaki a muryarsa, ta ɗan yi shiru sannan tace "eh. Uhmm, ko ka san wata Safina Ibrahim ne?" Sai daya ɗan ajiye wayar akan cinyar sa ya yi tsakin jin haushin kansa, why must he relate everything to Safiyya ne wai? Kawai daga jin Safina sai ya dangantata da yar uwar Safiyya? Ya sake daukan wayar yace "uhm. Sorry Please. Akwai wata Safina da na sani ne, in fact ita ce the only Safina dana sani. Though ita ma sunan ta kawai na sani. Yar uwarta ce wacce na sani" ya kuma ajiye wayar tare da dafe kansa "damn it. Must I talk about her?" Ya sake daukan wayar sai kuma yayi shiru gudun kar ya cigaba da maganar Safiyya. Tace "hello? Ina jin ka. I guess you know the sister very well ko? I want to know. Tell me" yace "there is nothing to tell. Just tell me about your self, like, yar wanbe gari ce ke? Kano?" Sai kuma ya sake jin haushin kansa. Tace "noo, not Kano. Ni yar Katsina ce" yace "really? But hausarki doesn't sound like hausar yan Katsina" ta danyi dariya "I get that a lot from people that don't know me. Bana son dialect ɗin so ina kokarin cire shi, musamman saboda duk makarantu na ba anan na yi su ba" yace "okay. Uhmm, I think that's all I need from you now. Please ki bawa Mufida number ɗin wani haka da za'a yi magana da shi, like your uncle or something. My family will contact them and do all the necessary stuff. That's all for now" Tace "all? I thought zaka ce zaka zo muga juna ko?" Ya girgiza kai "no. My family will meet yours and do all the necessary things. I will see you idan komai ya daidaita. But now I am very busy" ya ji bacin rai a muryar ta "amma idan da zaka zo ɗin zanji dadi sosai, you have no idea how much I waiting and prayed for this. And ko suma su Abba zasu fi bawa abin muhimmanci idan suka ga kazo gurina" yace "no, zasu fi bada muhimmanci idan suka ga elders dina sun zo gurin so. I am sorry but I cannot come" tace "okay. Then how are we suppose to know and understand each other?" Yace "I will call you when I need more informations" tace "how can you call me bayan baka da number ta?" Yace "ki karbi tawa a hannun Mufida ki kira ni" tace "how can I call you bayan kayi blocking number ta " ya rufe idonsa yana jin kansa yana sarawa yace "okay. I will collect your number and unblock you. Shikenan?" Tayi murmushin da yaji sautinsa a cikin wayar "shikenan, naji dadi sosai. You have......" Ya katse kiran ya jefar da wayar akan gadon tare da dafe goshin sa da hannu biyu. Zuciyar sa tafasa take yi, kokari take sai ta lissafo masa aibun yarinyar da suka gama waya da ita. Safina she said. But why? Upon all the names na mata a duniya why did she have to be Safina, bayan kuma Safinan ba wani suna ne irin wanda ya cika gari sosai ba. Yana ta so ya goge duk wani abinda zai ke tuna masa da Safiyya and then all of a sudden yarinyar da yace zai aura tana da sunan step sister din Safiyya. Safiyya used to talked a lot about her, ta kan ce "she is more like a sister to me, tare muka taso, a daki daya, a hannun uwa daya da uba daya". Lokuta da dama ya kanji su suna waya, and daga yadda suke hira suna dariya ya fahimci akwai shakuwa da kaunar juna  sosai a tsakanin su. Ya mike tsaye tare da daukan wayar ya fita. A parlor ya tarar da Mufida da Mama suna zaune suna hira, ya ajiye wa Mufida wayar a gabanta yace "ki samo wata. Na fasa wannan ɗin" Mama ta mike tsaye tana kallon sa amma sai ya dauke kai yayi hanyar fita, ta riko hannun sa ya dawo baya, tace "kai Muhammadu, dago kai ka kalle ni" ya kasa kallon nata amma sai ya samu guri ya zauna a gabanta "akan menene kace ka fasa" yayi shiru yana jujjuya kai still idonsa a kasa. Ta kara karfin muryarta "a bayanan da ta baka ne wani abu bai yi maka ba? Ko wata magana mummuna ta gaya maka wadda za'a iya fasa aure saboda ita?" Ya dago kai "Maaama! Ke ma fa ba sanin yarinyar nan kika yi ba kamar yadda ni ma ban santa ba. It wouldn't hurt anyone idan aka ce an fasa ɗin tunda dama ko maganar ba'a fara ba" ta koma ta zauna tace "I don't care much about her Gidado, in fact she lost some things a gurina tunda har ta iya fitowa social media tana neman namiji. But still that earned her something saboda hakan ya nuna tabbas tana son ka. And I do care about you a lot. I don't like hanyar da rayuwar ka take dauka akan mace. Now tell me, me yasa kace ka fasa auren ta?" Sai da ya dan yi jim sannan yace "sunan ta Safina" Mama tace "and?" Yace "sunan yar uwar Safiyya ne" Sai da ya fadi maganar sannan ya fahimci wautar da yayi, bai kalle ta ba amma a jikinsa yana jin mugun kallon da take bin sa da shi. Yayi shiru yana jiran yaji ta rufe shi da fada amma sai kuma yaji ta sake tambayar sa "Okay, ka tambaye ta kenan ta kuma tabbatar maka da cewa ita ɗin ce?" Ya girgiza kai "ba ita ba ce ba. Ita wannan yar Katsina ce su kuma yan Kano ne". Ya cigaba da jiran fada, amma sai yaji tayi ajjiyar zuciya tace "Gidado, Allah ya kwato min kai a hannun waccan matar. Allah kuma ya saka min abinda tayi min. Tashi kaje tun kafin kasa zuciya ta ta buga. Ba za'a fasa ɗin ba. In an samo wata kuma cewa zaka yi a cikin yan uwanta akwai mai suna Safiyya. Ko in anyi auren kazo kace kai ka fasa saboda suna da makociya Safiyya. Allah ya shirye ka". Ya mike ya fita, feeling silly. Ita Mama ba zata gane ba, shi a ganinsa wannan is enough reason to call the wedding off, dan shi duk abinda zai ke tuna masa da Safiyya gudun sa yake yi, shi kadai yasan abinda yake ji a ran sa. Sai after two days sannan ya karbi number ɗin daga gurin Mufida, shima Mufidan ce ta dame shi da maganar cewa Safina tana tayi mata maganar, da ya karbi number ɗin ma bai kira ba har sai bayan wasu kwana biyun da Mama ta yi masa magana "idan baka kira yarinyar nan ba wai ta yaya zaku samu fahimtar juna ne? Musamman considering baku da isasshen lokaci? Idan kuma da gaske ba zaka auren ta ba dan sunan yar uwar waccan mayaudariyar ne da ita to sai ka fada mana muji in yaso mu nemo maka wata a dangi, in ma kuma auren ne ba zaka yi ba gabaki daya shima sai ka fada musan cewa bamu isa mu saka ka ba". Da suka zo dinner da daddare ma sai da Abba yayi masa maganar" ka kira yarinyar can kuwa? Ya kuke ciki? Yaushe zaka je ka ganta?" Ya juya yana kallon Mama wacce ta tabe baki bata ce komai ba. Ya sunkuyar da kansa yace "zanje Abba, ina dan so in samu lokaci ne" Abba yace "lokaci? Lokaci kuwa ai shine babban abinda baka dashi. Shekara nawa muka baka? You have only two months my friend, ko ka je ku daidaita da wannan ɗin ko kuma wallahi kaji na rantse sai ranar daurin auren ka zaka san dawa aka daura. Stupid" Ya cigaba da jujjuya cokali a cikin abincin, sama sama yana jin Abba suna cigaba da maganar da Mama, tana gaya masa cewa yarinyar ta turo number din uncle dinta, Abba kuma yana nuna cewa ba za'a yi contacting dinsu ba har sai sun tabbatar cewa Gidado is fully committed dan kar suje suyi magana biyu. Gidado ya mike tsaye, Mufida ta rike hannunsa "hamma ba ka ci abincin ba" muryarta cike da damuwa, murya can ciki yace "am not hungry" sannan ya wuce ciki. Dakinsa ya shige zauna a kan kujera, staring into nothing, babu abinda yake gani idan ya rufe idonsa sai hoton Safiyya da ciki, cikin wani, waye wanin amma? Waye mijin Safiyya. Ya tuno da maganar da Mama ta fada sanda ya gaya musu cewa Safiyya tana da aure, she said wanda Safiyya take cewa Daddyn ta ne, wanda take zuwa kasar waje gurin sa, shine mijinta. Ya san pictures din Daddy, tabbas ya haife ta ko ma wadda ta fita, amma kuma yana da kuɗi, yana da bala'in kuɗi, yammata kuma a wannan zamanin sukan auri sa'an kakansu ma saboda kuɗi. But Safiyya doesn't look like a gold digger, she never sounds like a gold digger. He just couldn't picture her and that man as husband and wife. Yayi kokarin kawar da tunanin daga ransa dan gudun illata zuciyarsa. Ya fara mayar da tunanin kan issue at hand, issue ɗin wannan yarinyar Safina. He regretted cewa ya zabe ta. Bai san dalili ba but he just doesn't like her tun kafin ya ganta, kuma in zai gaya wa kansa gaskiya ya san aibunta kawai shine dan sunanta Safina, which is not fair to her. She couldn't possibly be Safinar Safiyya, like is not that cruel is it? Ya tashi ya koma kan study table dinsa ya bude laptop dinsa, in da akwai inda zai samu aibun yarinyar to tabbas a social media ne, anan zai samu abinda zai nuna wa iyayen sa yadda zasu yarda a fasa auren ba tare da sun jingina fasawar da Safiyya ba. Ya bude goggle sannan ya tsaya yana tuno sunan da ta gaya masa "Safina Ibrahim" amma da ya fara typing sunan sai ya samu kansa da typing "Safiyya Adam Muhammad" "damn it" ya faɗa a fili, subconsciously yana son yin bincike ne akan Safiyya. He saw a lot of results da basu da dangantaka da Safiyyan da yake nema, he saw her Instagram account with the few posts she made most of which na abinci ne. Yayi murmushi "acici" sai kuma yayi sauri ya fita ya cigaba da binciken sa amma bai ga wani abu da zai yi linking dinta da aure ba ko kuma ya yi directing dinsa to mijinta. Ya koma search engine din sannan yayi typing "Alhaji Adam Muhammad" a cikin results din ya ga wanda yake nema, ya gane hotonsa from the pictures dinsa da yake gani a wayar Safiyya. Anan yaga biography dinsa da aka yi publishing, ya shiga idanunsa suna searching abinda ya ke nema, anyi rubutun ne akan a lot of achievements dinsa da irin tarin arzikin da yake da shi da kamfanonin da ya mallaka, he was even listed a cikin manyan masu kuɗin Nigeria. Yayi ta wucewa har yazo kan abinda yake nema, a cikin biography ɗin nasa anyi listing spouses dinsa, sunan farko shine "Safiya" sai kuma "Sa'adatu". Ya kife fuskar laptop din da karfin da shi kansa ya san ta lalace. Ya mike sannan yayi jifa da kujerar da yake kai a zaune. Sai kuma ya zauna akan gado tare da rintse idanunsa. "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ya furta a hankali. How much more pain does he have to endure. How much more pain can his heart take. When will this end? Ya koma da baya ya kwanta yana kallon sama. Ba san me zai yi tunani ba, bai san me zaiyi ba, bai kuma san tsahon lokacin da ya dauka a haka ba. Daga baya ya koma ya zauna sannan ya jawo wayarsa ya bude number ɗin Safina sannan ya kira. Ba'a jima ba aka dauka "alhamdulillah. Allah shine abin godiya. Tunda nayi sallah nake zaune akan sallaya ina gaya wa Allah bukatu na akan ka. Gashi kuma ban tashi ba sai da Allah ya amsa min ya juyo min da hankalinka gare ni". Yace "listen Safina. If we are going to do this, then we are going to do it the right way. I am really heartbroken right now. I am in love, deeply in love with someone else, someone that I cannot have. Wannan ne dalilin da yasa aka matsa min akan auren nan. Bana son shiga hakkin duk wacce zan aura, so I want you to know what you are getting yourself into. Babu rufa rufa. I will marry you saboda ina son in farantawa iyayena rai, but chances are I might never love you, or anyone else. Me kika ce? Kin amince?" Sai da tayi shiru na wasu lokuta, daga dukkan alamu maganar ta sa ta dake ta sosai. Sannan tace "I don't know what tomorrow will present to us. Babu wanda ya san gobe. Yanzu na sani, abinda na sani a yanzu kuma shine ina son ka, ina matukar son ka. Na kuma san cewa in na aure ka zan baka dukkanin kulawar da miji yake bukata daga gurin matarsa. Na kuma san cewa ita zuciya an halicce ta ne a bisa son mai kyautata mata, so chances are high that you will love me. Maybe one day in ka tuna da waccan har sai kaji haushin kan ka ma kana tunanin what made you love her. So yes, I am going to take my chances. Na amince, a bisa alkawari guda daya, cewa you will try your best akan sauke dukkan nauyin da addini zai gindaya a tsakanin mu. Kuma ba zaka wulakanta ko goranta min soyayya ta ba". A cikin sati biyu aka gama bincike, kuma a iyakacin abinda aka samu babu wani abu da zai hana aure a musulunci. An gano asalin ta, an kuma yi bincike akan tarbiyyar ta. Daga nan uncles din Gidado, Uncle Habib, Faruk da kuma mijin aunty dinsa Maimunatu suka je har Katsina suka nema masa aurenta, a take kuma kanin mahaifin ta ya basu auren ta. Aka saka rana sati shida yadda zai zo dai dai dana Mufida kamar yadda iyayen angon suka nema. Daga nan kuma sai aka cigaba da gudanar da shirye shirye a duk bangarorin biyu. ****.     ****.    ****.    ****.    ****     **** *Her🧕🏻* Sama sama muka yi magana da Mukhtar, nayi kuma iyakacin kokari na na ganin cewa banyi masa wulakanci ba tunda yanzu ni ce da kaina na neme shi, sai dai kuma na katse maganar da cewa akwai abinda nake yi amma zan kira shi idan na gama. Na mike ba tare da na kalli Abdul ba nace "zan shiga ciki, thank you for...... For listening" ya mike shima "amma da zaki ji shawara ta kar ki koma ciki yanzu, ki dan basu space ki bari su huce tukunna. Ke ma ki huce" na tsaya amma ban ce komai ba, ya mike shima "let me take you home" na juyo "ba gidan ku zamu koma ba, mun samu gurin zama for the time being" yace "I know, amma zaku dauko kayan ku daga gidan na mu ai ko? Let me take you there sai ki debo muku kayan ku". Ban cigaba da musu ba saboda nima bana son komawa gurin Mommy da Daddy a lokacin. Muka shiga motar sa muna tafiya a hankali na jingina kaina a jikin window tare da rufe idona, hoping ina ma dai mutum yana iya hana kansa tunani? Na jima a haka sannan naji yace "Fiyya. Wata tambaya nake son yi miki. Ban san yadda zaki dauke ta ba. Please kar ki ji haushi bana nufin komai sai alkhairi. I will only ask the question dan naga yau mun samu fahimtar juna. You can choose not to answer it if you will" na dago kaina tare da bude ido nace "ina jin ka" kamar ba zai yi magana ba sai kuma yace "akan wannan da kika gaya min kina so, shine baban babyn ki?" Nayi sauri na kalle shi. Ya daga hannu "am sorry. In ba kya son amsawa forget I ever asked it" na juya kaina na cigaba da kallon gefe, sai da na jima a haka sannan nace "ba nashi ba ne ba. But kasan wani abu? Sometimes in akayi min irin wannan tambayar I wish cewa nashi ɗin ne. It would have made everything easier for both of us. Da sai dai Daddy yayi fadan shi ya gama, maybe ma ranshi ba zai kai yanzu baci ba, shima nashi iyayen in suka ji ransu ya baci suyi fada, but duk kan su ba zasu iya disowning din mu ba saboda suna son mu, at the end zasu nema mana mafita ne, which would be to get us married, muyi aure mu rike babyn mu, and live happily ever after. The end". Ban jima a gidan Aunty Hajjo ba na gama hada mana kayan mu, tare muka tafi da ita zuwa gidan da Daddy ya kama mana muka danyi gyare gyare kafin su Daddy su zo. Ita ta kira Mommy ta gaya mata muna tare. Da furnitures da komai a gidan dan haka kayan sakawar mu kadai muka shiga dashi, sai yan few abubuwan da naga babu nayi mana order za'a kawo mana har gida. Tunda su Daddy suka zo daga shi har Mommy babu wanda ya kula ni, Mustapha ne ya kai shi dakin da aka shirya domin shi sannan ya shirya masa kayan sa da duk abubuwan bukatar sa. Ni dai da naga na gama abinda zan yi kuma babu wanda yake yi min magana sai na wuce na tafi dakin da yake a matsayin nawa nayi kwanciya ta. Sai dare sannan Mommy ta shigo. "Ki tashi ki ci abinci" tace min. Na mike zaune kawai bance komai ba, sai ta zauna a bakin gadon tana kallo na tace "Safiyya wannan ita ce magana ta karshe da zanyi miki a kan auren ki. Duk da cewa yanzun ma ba wai zanyi miki maganar bane ba dan ina saka ran zaki chanja ra'ayin ki ba, zanyi ne kawai dan in nuna miki irin yadda rai na ya baci akan maganar. Ba kiyi halacci ba Safiyya, daga ke har mahaifinki ba kuyi min halacci ba wallahi. Ai na san kin san komai, duk da dai ni ban taba zama na gaya miki ba dan bana son ki dauki maganar kamar gori amma na san duniya ta gaya miki, kin san irin halaccin da nayi wa Safiya, ni na dauke ta a matsayin yar aiki sannan na mayar da ita mutum, duk abinda Safiya ta zama a rayuwar ta wallahi ni ce sila. Haka kema kuma, tun kina zanin goyon ki na dauke ki na rike tamkar nina haife ki amma yanzu ni ce abin gudu a gurin ki. Shi kuma mahaifin ki ya goya miki baya as always. Babatun sa da fadansa na banza ne in dai a kanki ne baya iya juya ki sai abinda kike so shi kikeyi. Ba'a saka ki ba'a hana ki. Kuma kowa ya dan dalilin da yasa kika samu kanki a halin da kike ciki kenan. Amma har yanzu bai dauki darasi ba. Da wasu iyayen ne ma har wanni zaɓi za'a baki? Bayan abinda kika aikata kuma ace sai an baki zabin mijin da zaki aura? Da wasu iyayen ne da tuni baki fadi uban shegen cikin ki ba? Kuma na san abinda zakuyi nan gaba, tunanin ku yanzu shine in an haifi shegen a dauko shi a kawo min ace in rike shi saboda ni ce karkatacciyar kuka mai daɗin hawa ko?. To wallahi kar ku sake ku doso ni da shi ma. Na fada miki wannan ne dan ki sani, zan cigaba da sauke nauyin ku da Allah ya dora min daga ke har mahaifin ki amma na daina going extra for any of you. Na daina saka bukatun ki a saman na ƴaƴan da na haifa da cikina. Tunda kun tabbatar min da cewa bani na haife ki ba. Kun tabbatar min da matsayina na matar uba kuma na dauki matsayin nawa". Har ta gama bance komai ba, tana gamawa ta mike ta bar dakin ni ma kuma na koma na kwanta na cigaba da kallon ceiling. Shin da gaske na yiwa Mommy butulci? Haka rayuwa ta cigaba da tafiyar min, har tsahon sati uku, Mommy ta janye jikinta sosai daga gare ni haka Mustapha ko magana baya yi min, nima kuma dama ba so nake yayi min maganar ba, Daddy ma kamar ko da yaushe sama sama yake min magana in dai har munyi doguwar magana to faɗa ne. Kullum dakina ne gurin zama na akan sallaya ta, anan nake sallah ta, anan nake kuka na, anan kuma nake bacci na. Na cigaba da zuwa asibiti ganin likita, na tabbatar masa da ra'ayi na na bayar da ɗan cikina for a closed adoption idan na haife shi. A ranar da muka cika sati uku a gidan ne bayan na tashi da safe na fita da niyyar gaishe da Daddy da Mommy kamar yadda na saba kullum, ina fita parlor sai naga Daddy shi kadai a zaune akan electric wheelchair dinsa da kofin tea a hannunsa. Na karasa na gaishe shi ina lura da bacin ran da yake bayyane a fuskarsa, a raina har na fara lissafin ko nayi wani sabon laifin ne. Amma sai naji bai yi min faɗa ba bayan amsa gaisuwa ta da yayi. Na mike ina dube dube. Na shiga kitchen na fito na kuma shiga dakin su Daddy na fito amma ban ga Mommy ba. Daddy naji yace "she is gone" na juyo ina kallon sa. "Gone? Gone where?" Yana kallona shima yace "home. Sun tafi Nigeria ita da Mustapha. Wai auren Safina za'a yi. Safina ce wai aka bayar da ita ba tare da ko faɗa min anyi ba. Suka shirya tafiyar su ba tare da sun gaya min ba. Sai da safe kawai suka fito da akwati wai Nigeria zasu tafi bikin Safina. She said wai na nuna mata cewa ke ba yar ta bace ba shi yasa ita ma ta nuna min cewa Safina ba yata ba ce ba". Not edited. Forgive the typos please. [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹 Safiyya ❤‍🩹* *By* *Maman Maama* *Episode Ten: Soul Mates* Free Episode Na zame na zauna akan kujera cikin mamaki "aure Daddy? Safina ce zata yi aure amma ni ban sani ba? How? Why? To wa zata aura ma?" Yace "ba ta gaya miki ba kema? Kuna magana kuma?" Na gyada kai. Na san mun dan samu falling out da Safina kwanan bayan nan, and must issue din mu na san laifi na ne saboda yadda na zama very rude to her a watannin nan, hakan kuma yan ada dangantaka da mood dina da kullum bashi da kyau. Amma ban dauka har zata iya yin aure ba tare da na sani ba. And ko shekaran jiya munyi chats da ita. We even talked about magana ta da Mukhtar. Nace "muna magana Daddy, amma ko alama bata nuna min ba. Wa zata aura kuma?" Ya girgiza kai "ban sani ba, they didn't tell me and I didn't ask tunda sun nuna ban isa ba. Ba ki san samarin ta ba?" Na yi shiru ina tunani "Safina bata da saurayi. Ni dai ban san wani saurayi da take kulawa ba" na tuno da yadda takan takan yi min kallon zautacciya duk sanda muke tare in taji muna waya da Gidado. Tace soyayya irritating dinta take yi. "How can she do that?" Na fada a fili. Daddy yace " ba laifin ta bane ba. Am sure Sa'adatu ce zata hana ta fada dan tana so ta bata min rai, tana so ta nuna min nata ikon" nayi ajjiyar zuciya "babu komai Daddy kar ranka ya baci, we don't need them. We can do this alone. Su je suyi mata aure, Allah ya sanya alkhairi. All we have to do now is hire someone, kamar a nurse haka that can take care of you, sai kuma mu nemi a house keeper da zata ke shigowa ko da twice a week ne tana kula da gidan, and I can drive, duk inda zamuje zan iya kai mu" yayi shiru yana kallo na da murmushi a fuskarsa, sai kuma ya girgiza kai "Safiyya kenan. Kin dauka damuwa ta kenan? Wanda zai kula da ni? Damuwa ta shine wanda zai kula da ke idan babu ni. I don't want any enmity between you and them saboda ko babu dangantaka ta jini su yan'uwanki ne, ba na son in babu ni ki rasa wanda zaki yi turning to. Ke ba yanuwan uwa ne da ke ba, and in akayi auren ki da Mukhtar yan uwans sun zama na mijin ki, ke ba older siblings ne da ke ba. In na mutu ya zaki yi?" Na koma na zauna ina jin wani kadaici yana lullube ni. Tamkar Ni kadai ce a duniya. Ya cigaba "shi yasa da farko naso auren ki da Mustapha, at least it will strengthen the bond between you kuma ba zasu yi spilling secrets dinki ba. And you will still have Ahmad a matsayin uba ba matsayin uban miji ba, zai kuma saka ido ya ga cewa basu cuce ki ba. But now, now I don't know what to do sai dai addu'ar Allah ya kara ara min lokaci" Na gyara zama "amma Daddy ba ka ganin wannan tafiyar da suka yi suka barmu ta nuna true intentions ɗin su? Ta nuna cewa ba soyayyar Allah da Annabi suke yi mana ba?" Yace "Allah kadai ya san abinda yake ran bayin sa. I don't know abinda ke ran Mustapha, amma na san Sa'adatu is not cruel, stupid but not cruel, she is just scared that she will loose everything" nayi kokarin gane maganar amma ban fahimta ba sai na chanja magana "I still have the twins" yayi murmushi "yes, and they are the more reasons why dole in gyara tsakanin ku kafin in bar duniya, if not, you will loose them too, dan babu yadda za'a yi su juya wa uwarsu baya saboda ke". Daga nan na tashi na shiga kitchen na hada wa kaina smoothie na zauna ina sha ina jimamin abinda ya faru, har lokacin na kasa yarda wai da gaske Safina ce zata yi aure amma wai daga ni har Daddy bamu sani ba, kuma naji a raina babu abinda nake son sani irin wanda zata aura ɗin, waye shi? Yaushe suka hadu? A ina suka haɗu? Nayi kokarin mantawa da abin in fuskanci abinda yake gaba na amma sai naji na kasa. Na koma daki na dauko waya ta na kira Hassan, dole ai na san twins zasu sani musamman tunda suna Nigeria. Hussein ne ya sauka da murna a muryarsa ya gaishe ni "yaya da ke za'a taho? Kun fasa zama acan din? Mun dauka ai cewa kuka yi sai kin haihu zaku dawo Nigeria" nace "no Hussein ba dani za'a taho ba, kun yi waya da Mommy kenan?" Yace "eh dazu ta kira mu tace gasu nan zasu taso. I thought gaba daya zaku taho ai" nace "a'a, ita da Mustapha ne ka dai, ni da Daddy muna nan" naji chanji a muryarsa "but why? Me yasa zasu taho su barku ku kadai? Gashi Daddy babu lafiya ke ma kuma haka?" Nace "Mommy tace bikin Safina za'a yi. Kun sani?" "Bikin yaya Safina?" Ya mayar min da tambaya ta, nayi ajjiyar zuciya, basu sani ba suma, ya sake tambaya "wa zata aura?" "I don't know Hussein. Actually abinda na kira ku in tambaya kenan, daga ni har Daddy bamu san komai akan auren ba, and it hurts ne that bamu sani ɗin ba" ina jin sa yana magana da Hassan a kusa da shi, sai Hassan ɗin ya karba ransa a bace "but this is not right. Kawai tace mana zata je Katsina tun last two weeks kuma har yanzu bata dawo ba. She didn't tell us anything" nace "babu komai. In sun karaso kwa tambaye su details din sai muji" ya cigaba da fada sai na kashe wayar dan nasan idan ya fara ba dainawa zai yi, shima yayo gadon zuciya irin ta su Daddy. Daga nan kuma sai na mayar da hankali na gurin sama mana solution ni da Daddy, na kira Abdul na nemi taimakon sa na gaya masa abinda nake bukata, ina son a samo wa Daddy nurse namiji da zai ke taimaka masa with his day to day activities, sannan kuma da house keeper macw da zata ke shigowa two times a week tana gyara gidan, ni zan iya girki da dan sauran kananan aiyuka. Shima yayi mamaki da yaji cewa su Mommy sun koma Nigeria. Zuwa yamma sai gashi nan shi da Uncle Lukman sunzo, suka zauna a gurin Daddy har dare sannan uncle Lukman ya tafi ya bar Abdul ya kwana da Daddy, sai da safe sannan nurse din da aka yi hiring yazo. Aunty Hajjo ta kira ni tace in koma gurinta amma sai na nuna mata nafi son zama anan tare da Daddy, ina son inyi spending as much time as I can with him. Kuma naji daɗin days that follows dan na samu ina dan motsa jikina wajen zirga zirgar kula da bukatun mahaifina, abinci sai inyi masa kala biyar a rana, mu kan ci tare sometimes, in kuma yan fadan sunzo ya balbaleni da fada sai in tashi in shiga daki, daga baya sai na fahimci ganin cikin jikina ne yake triggering fadan sa, sai na koma yin iyakaci kokari na wajen ganin na saka kayan da zasu boye cikin. Kwana hudu da tafiyar su Mommy Safina ta kira ni. Ni tunda su Mommy suka tafi ban kuma yi mata magana ba ko a chats ita ma haka. Ranar sai ga kiran ta. Kamar ba zan dauka ba dan in kara nuna mata bacin raina amma kuma curiosity ya saka na dauka. "Kinyi fushi ko kanwata?" Nace "ohh dama kina da kanwa a duniya? I thought yan Katsina ne kawai yan uwanki" tayi dariya "wallahi ba laifi na bane ba, Mommy tace kar in gaya miki dan kar ki gaya wa Daddy, tana fushi dan yaki yarda da auren ku da yaya Mustapha. Sai yanzu nace mata ni dai zan miki magana, tsakanin su daban tsakanin mu daban" cikin bacin rai nace "but how can you do that Safina. Ni ban damu da rashin gaya min da baki yi ba amma Daddy fa? Daddy fa Safina. Ace wai ba za'a gaya masa maganar auren ki ba?" Tace "na gaya miki ba laifi na bane ba" nace "but you can convince her otherwise, ko kuma kibi ta wata hanyar da za'a sanar da shi" tace "what do you want me to do? Yanzu sai kawai in kira Daddy in ce masa anzo neman aurena an saka rana?" Na girgiza kai "a gani na Daddy yafi karfin haka a gurin ki, a tunani na duk wanda zaki aura gurin Daddy zai zo ya nemi auren ki sai ya amince sannan shi zai kai shi gidan ku na Katsina" tace "to yanzu dai an riga an yi an gama. Ni dai ke zaki taya ni bawa Daddy hakuri dan Allah. Nasan in yayi fushin sa ke kadai kike sauko da shi" nace "ni ba zan shiga cikin wannan maganar ba, nima lallabawa nake yi dan laifuka na sun fi na kowa yawa a gurin Daddy". Daga baya dana tambaye ta game da wanda zata aura sai ta bani labarin cewa a waya suka haɗu, kawai friend request ya turo mata tayi accepting shikenan cikin kankanin lokaci suka fara soyayya, ashe dama a gidan su kuma an fara matsa masa ya fitar da mata, shine ya fitar da ita. Nayi mata murna tace "I can't wait for you to meet him. I am sure you will like him". Bayan mun gama wayar da ita na tashi na shiga wanka, bayan na fito sai na samu kaina da tsayawa a gaban mirror ina kallon kaina ina tunanin yaushe rabon da in kalli kaina a madubi? Zan iya cewa ma ni har na manta da kamanni na. Na lura da yadda nayi baki na rame sosai idunwana suka faɗa ciki, duk glow din fata ta yayi diminishing. Ga uban ciki na da sai kara girma yake yi abinsa. Na dora hannu akan cikin ina kallonsa a madubi, Allah ne kadai ya san irin azabar da cikin nan ya bani tun daga samun sa har zuwa wannan lokacin, laulayi babu irin wanda ban sha ba, ciwo babu irin wanda banyi ba, azaba ta duniya kam na ganta akan cikin nan. Na tuna da Fiyyan da da irin gatan ta da irin shagwabar ta, na hango ina ma ace da aure na samu wannan cikin, da auren Muhammad. Na lissafo irin shagwabar da zan zuba masa ina jin ko bandaki ma sai ya goya ni ya kaini, na hango irin son da Daddy zai yi wa abinda yake ciki na, watakila ma sai ya kwace min fada a gurin sa, na hango irin son da Muhammad zai yi wa cikin nan da ace nashi ne, nayi murmushi ina tuna kalamansa, kullum baya rasa aabinda zai fada da zai referring to auren mu ko yayan mu, kullum in yana so ya tsoka ne ni sai yace zai gaya wa yayan mu abinda nake yi masa. Na tuno sanda ya gane ina tsoron asibiti yace duk ranar da zan haihu za'a sha drama. I wondered idan da munyi aure da yaya haihuwa ta zata kasance a gidan sa, maybe tare zamuyi labor, ko kuma doctor ya kora shi waje dan in ina ganin sa a gurin kara rikicewa zanyi. "ai kuwa ba zai fita ba" na fada a fili, dan karamin hauka zaiyi musu. Nayi murmushi. Sai kuma na bata rai ina tuna reality ɗina, I lost everything. The person who raped me took away not only my virginity but my everything, bai barni da komai ba radadin zuciya marar misaltuwa. Ni yanzu ba komai bace ba sai fanko, an empty shell without hopes and dreams, without even a zeal to live, without hope for a future. Karar wayata ta dawo dani cikin hayyaci na, na goge hawayen da ya sauko kan kuncina sannan na kalli screen din, sunan Mukhtar na gani. Na dauke kaina gefe ina cigaba da kallon reflection ɗina a madubi. I hate breaking his heart every time amma shi ya kasa ganewa, ya kasa fahimtar cewa dan nace na zabe shi ba wai yana nufin ina sonsa ba ne ba, na zabe shi ne dan bani da wani option left. I sometimes wondered ya auren mu zai kasance da shi, dan ni bani da burin komawa Nigeria ko da na rabu da cikin nan, too many memories. Ya sake kira. Na dauka na saka a kunne na bance komai ba "Habibty" ya fada, nayi shiru ban ce komai ba "ko bacci kike ne na tashe ki" nace "uhm uhm" "ko ba kya jin dadi?" Nace "uhm" "okay bara in barki ki huta. I just want to check on you inji ya kuke, wallahi bana jin daɗin zaman ku ku kadai daga ke sai Daddy, so nake in taho amma Abba ya hana ni, yace in bari sai kin haihu tukunna sai in taho. And guess what? I think suna shirin zasu daura auren nan ne kina haihuwa, maybe shi yasa yace in bari, watakila sai a ango zan taho". Naji kamar in rushe da kuka amma na cigaba da rike wayar a kunne na. Ya cigaba "ke har yanzu baki gaya min plans dinki ba for the wedding. Su Abba sunce daurin aure kawai zasu yi, ba sa son anything that will call attention na mutane kan mu, amma ni ina son ki samu everything da kike da burin yi a auren ki. Amma baki taba fada min ba ko akwai wani abu special da kike so?" A hankali nace "ni babu abinda nake so. In an daura auren kawai shikenan". Ya danyi shiru "i know ba kya so na, but this is not about me but about you. I want you to have all your heart desires. I know mata da son biki, am sure you had plans....." Na katse shi "mata daban daban ne ai, kowa da akwai abinda take so. Ni bana son biki. Bana son yin komai" na fada ina jin raina yana kara baci. Ya sake yin shiru. Sai kuma a hankali yace "I am sure da shi zaki aura da baki bata rai dan ance ki fadi events din da kike son yi ba. I am sure da Gidado ne da kin fi kowa murna........" Na mike tsaye kamar wadda aka yi wa allura "don't" na fada cikin sarkewar murya, "don't you dare mention his name ever again" ya danyi dariya kaɗan "okay, okay. Na daina. I just want you to talk kin barni ina ta magana ni kadai shi yasa na dan taɓa button ɗin da yake activating ɗin ki. Amma nima kishi na ba zai barni in kuma ambatar sunan sa ba. Kin san...." Na kashe wayar nayi jifa da ita kan gado sannan na koma na zauna tare da dafe kaina, wani irin bacin rai nake ji, wani irin ciwo zuciya ta take yi min. Na san Mukhtar ya san Gidado kamar yadda shima Gidadon ya san shi, amma basu taba magana da juna ba kuma wani daga cikin su bai taba yi min maganar dayan ba. Ban san mai yasa jin sunan Gidado a bakin Mukhtar ya bata min rai har haka ba. Na jawo wayar tawa ina kallon hoton kan screen din. Hannun Gidado ne a ajjiye akan steering motar sa "Allah sarki Muhammad" Na fada a fili "Allah ka dubi bawanka". Na sani, ina son Muhammad son da ba zan iya kwatanta shi ba, na kuma sani shima yana min son da ban taba ganin irin sa ba. Na tuno da haduwar mu ta uku, na tuna da yadda ta kasance. ****.     ****.     ****.    ****.    ****.    **** Tunda muka rabu da shi a ranar da muka yi haduwa ta uku zuciya ta bata samu sukuni ba, naji haushin sa sosai a ranar, haushin rashin karbar number ta da baiyi ba, na kuma ji haushin kaina akan me yasa ni ban karbi tashi ba tunda shi ya manta bai karni tawa ba? Amma kuma ni nasan kaina, nasan pride ɗina na ƴa mace ba zai barni in karbi number ɗin saurayi ba ko kuma inyi making first attempt, na san cewa na kamu da son sa, duk kuwa da cewa a lokacin ban san so ba amma nafi so ace shine da kansa ya fara ambata min yana sona ba ni ba. Wani lokacin kuma in ina tunanin sa sai inji haushin kaina, ina ganin kamar shi bashi ma da interest a kaina shi yasa ma bai karbi number ɗin ko kuma ya nemi address dina ba. I mean wanne saurayi ne zai ga budurwar da yake so suyi magana sosai kuma har su rabu amma bai karbi number ɗin ta ba, who does that? Tun ina daukan abin wasa har ya zamar min gaske, kullum in ina zaune ni kadai shi nake tunawa, sai inyi ta bitar maganganun mu a raina ni kadai ina murmushi. In kuma na kwanta bacci Muhammad sai ya bini cikin bacci na, amma a baccin nawa yana karbar number ta har ya kira ni a waya muyi ta hira, ina ta murna, sai na farka sai inga ba haka bane ba. Lokacin dama Daddy ya kawo ni Abuja da niyyar uncle Ahmad ya nema min jami'a a cikin manyan jami'o'in Abuja saboda in samu in zauna a guri daya in daina binsa ƙasa ƙasa, uncle Ahmad ɗin kuma yayi kokarin samar min admission ɗin, jira kawai yake a fara registration ya kaini inyi, a lokacin ne wata dabara tazo min. Ina tunawa a cikin maganganun da muka yi da Muhammad ya fada min family dinsa sun bude sabuwar jami'a in honor of his late grandfather. Ya kuma shaida min yana son yin aiki a can. Duk da dai lokacin da muka yi maganar bai fara aikin ba. Sai na yanke shawarar why not in saka a nema min admission a makarantar, maybe mu sake haduwa a can. Maybe ma in ganshi a aji a matsayin malami na. Na tuna sunan makarantar "MD University". Naje na samu uncle Ahmad da maganar "uncle wata sabuwar jami'a da aka bude kwanan nan, MD University, can nake so a nema min" ya bata rai "ban gane ba. Ita kuma wannan da aka nemar miki menene matsalar ta?" Nace "babu komai uncle, kawai dai ni nafi son waccan ne, akwai kawayena da suka ce min can zasu je, kaga zan samu abokan karatu". Haka nayi ta bugawa amma uncle Ahmad yaki yarda, ranar nan ma cewa yayi in na sake yi masa maganar sai ya kwada min mari. Mukhtar yana ta yi min dariya. Ni kuma naki hakura dan gani nake makarantar ita kadai ce chance ɗina na haduwa da Muhammad again. A haka Allah ya kawo savior dina kasar, Daddy, ai kuwa ranar da yazo da maganar na tare shi, "Daddy ni MD University nake son a nema min, ni bana son wannan da aka samu" ya juya yana kallon uncle Ahmad "wacce ce kuma MD?" Uncle Ahmad yace "kar ka biye mata yaya, wata sabuwar jami'a ce da ko kafuwa bata yi ba ballantana musan kyanta ko akasin haka. Wannan shekarar fa suka fara daukan daliban su na farko" na zamo daga kan kujera na fara kuka "ni wallahi Daddy ita nake so. Dan Allah ni dai a kaini can. Allah in ba'a kai ni ba ba zanyi karatun ba" Daddy ya fara fada "ba za'a kai ki ba ɗin. Wannan da aka samo ɗin ita zaki je". Amma daga ni har duk wanda yake gurin mun san cewa kamar an kai ni ne an gama. Wata guda bayan nan har na gama registration na fara zuwa lectures. Tun daga nan kuma sai na fara abinda ya kai ni makarantar, neman Muhammad. Farko na fara neman sa a cikin malaman department din mu, amma ban same shi ba, sai na fara nema a na sauran departments amma na rasa a ina zanyi concentration neman tunda ni ban ma san me ya karanta ba ballantana in san me zai koyar. Sai na fara shiga cikin yan wani department din da ba nawa ba, in ana hira sai ince something like "ai naji labarin wannan malamin naku Muhammad Lawan, ance bashi da kirki" and they will be like "mu bamu da malami Muhammad Lawan" and I will be like "Okay ba department din ku bane ba ashe". A haka har sai da na fara fitar da rai, thinking ko ya chanza shawara bai karbi aikin ba. Amma kuma na kasa hakura. A haka har semester ta kare aka fara shirye-shiryen exams. A lokacin ne kuma naje zanyi submitting wani assignment ɗina a office ɗin wani malamin mu. A lokacin ne kuma na ganshi. Building din hawa biyu ne, duk offices din lecturers ne, office ɗin wanda zan kaiwa yana sama, ina hawa hawa saman idona ya sauka akan Muhammad a kofar wani office yana budewa. Sai dai bai ganni ba ya bude ya shiga ciki sannan ya mayar ya rufe. Na karasa da sauri ina jin wani irin excitement amma kuma zuciya ta tai yarda da cewa shi din ne. Naje kofar office din da ya shiga na tsaya na karanta sunan jikin office din "Muhammad Lawan Muhammad" naji wani dadi ya rufe ni kamar in taka rawa a gurin. Amma kuma what next? Gani dai gashi, katanga ce kawai a tsakanin mu amma me zanyi kenan? Shin zanyi knocking ne in ya buɗe ince hi? Ko kuma shiga kawai zanyi inyi pretending kamar batan kai nayi ba nan zan shigo ba, in yaso sai in nuna mamakin ganin sa a office ɗin. To amma kuma ai ga sunan sa nan baro baro a jikin kofar, in na shiga dole zai gane neman sa nake yi. Na dafe kaina, ga koshi ga kwanan yunwa. A karshe haka ina ji ina gani na wuce office din ban shiga ba naje nayi submitting assignment dina na sake wucewa na koma gida. Amma hankali na ya kwanta tunda na ganshi na tabbatar yana makarantar, sai na kudiri aniyar zan san yadda zanyi ya ganni kuma ya fara yi min magana. Daga nan na fara monitoring dinsa, na lura da sanda yake shigowa makarantar da kuma sanda yake fita. Sai na shirya plan dina. Sai da na daidaici lokacin da yake fita sannan na kwashi littattafai da takardu na tafi kan stairs din offices din nasu na baje wai ni lallai karatu nake yi. Ina zaune da uban takardu a gaba amma hankali na yana kan duk motsin da za'a yi a sama. A haka har na ji taku, na dan duba ta gefen ido na ga shine sai na dauke kai na cigaba da bude littafin gaba na amma ina jin zuciya ta tana ta bugawa da karfi. Ban ankara ba sai gani nayi yazo ya wuce ni ba tare da ko kallon inda nake yayi ba, yaje ya shiga motar sa ya tayar ya fice daga makarantar. Naji takaici ya kama ni. Amma na gaya wa zuciya ta cewa bai gane ni ba musamman saboda bayana zai gani sanda yaje saukowa. Sai na chanja shawara. Washegari takanas na samo kujeru guda biyu da dan karamin table na dasa a direct opposite stairs din su. Na baza takardu sannan na sawa kofar office ɗin sa ido, a haka har naga ya fito ya rufe kofa sannan ya fara saukowa, sai da naga ya kusa gama saukowa sannan nayi dabara na zubar da takardun gaba na, kamar irin iska ce ta zubar da su ɗin nan, ko bai ganni ba na san hasken takardun zai dauki hankalin sa. Naji takunsa ya doso inda nake, ina jin kamar a cikin zuciya ta yake taka kafafunsa, sai kuma ya tsaya a dai dai sai ti na. A lokacin na tabbatar cewa ya ganni kuma ya gane ni amma ban kalle shi ba sai na cigaba da bude pages din littafin da yake gaba na. Naji Muryar sa "oh my God" still ban daga kai ba. Ya kara matsowa "oh my goodness. Piya? It is really you" na dago kai ina bata fuska, sannan na bishi da kallo tun daga kan takalmin kafarsa zuwa fuskarsa da take reflecting wani irin annuri da farin cikin da zuciyar sa take ciki. Na bayyana mamaki a tawa fuskar "wow. Malam Muhammadu dan fillo. What are you doing here?" Ya ja kujerar da dama dan shi na ajiye ya zauna "ke zan tambaya Piya, what are you doing here? How comes? Taya kika zo nan? Shin ko mafarki nake yi ne?" Nayi murmushi ina nuna masa takardun gaba na "karatu nake yi. Anan makarantar nake. Kai fa?" Yace "I work here. Ga office dina can. I can't believe this. You have no idea yadda na sha wahalar neman ki a garin Abuja" a raina nace "taka wahalar ka sani ba ka san tawa ba". Yace "ranar nan was the best and the worst day of my life. I can't believe I let you go ba tare da na karbi number ɗin ki ba. I went back to your car na zauna jiran mechanic dinki yazo daukan mota in karbi number ɗin ki a hannunsa, amma that good for nothing mechanic bai zo ba, anan nayi sallar la'asar da magrib" na rufe bakina ina dariya, shima yayi dariyar "stop laughing at me. Nasha wahala fa. Har dare bai zo. Da sassafe kuma dana koma gurin already har ya dauke motar". Nace "to ai Allah ya yi yanzu, gashi mun sake haduwa" bai ce komai ba sai ya dauko wayar sa ya ajiye min a gaba na "i won't repeat the same mistake. Dauki ki saka min number ɗin ki" na dauka na saka, na mika masa amma sai yaki karba yace "save it" nace "okay, me zan saka maka yadda zaka gane. Safiyya Adam Muhammad kamar yayi tsaho, ko in saka maka Fiyya?" Ya girgiza kai "Piya. You will always be Piya to me" nayi murmushi ina jin zuciya ta fari kal. Nayi saving da Piya💝 na mika masa still sai yaki karba yace in kira, sai dana kira ya tabbatar ta shiga sannan ya karbi wayarsa. Na dauko tawa wayar a jaka nayi saving tasa number ɗin, farko na saka Muhammad, sai kuma na goge na saka "Pyar💝" Forgive the typos Say Hi to this number so that your number can be saved. We are almost done with free pages insha Allah. 0704 203 0419 Yan kasuwa kofa har yanzu a bude take. Advert your markets with Safiyya and Gidado.[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹 Safiyya ❤‍🩹* *By* *Maman Maama* *Episode Twelve: Twisted* Free Episode Masu bude telegram musamman saboda su karanta Safiyya, you guys have a special place in my heart. I really appreciate the love and support. Dan ku na kasa daina rubutu 😍💕 Gidado yayi taku biyu baya yana kallon hannun da mutumin ya miko masa, sai kuma ya kalli fuskarsa kamar mai kokarin gane wani abu "Mustapha? Mustapha kace" mutumin ya sauke hannun sa ganin gidadon bai yi shaking ba, Al'ameen yace "eh Mustapha yace, ka san shi ne?" Wani murmushi Gidado yayi, a zuciyarsa yana jin kamar an dauke masa wani babban dutse, yace "no. Ban san shi ba. At least not yet" mutumin ya mayar masa da murmushin sa yace "Yes. I believe we will soon know each other a matsayin in laws". Yayi gaba su Gidado suka bishi a baya zuwa mota, sai a lokacin suka lura da cewa su biyu ne suka zo. Suka gaisa da dayan shima sannan suka shiga bayan motar su kuma suka shiga gaba, wanda ya kira kansa da suna Mustapha yana driving. Gidado ya juya kansa yana kallon waje yana jin daɗin iskar da take dukan fuskar ta sa, iskar yanci. Yanzu tabbas yana da tudun dafawa. Safiyya tana yawan ambaton Mustapha a maganganun ta kamar yadda take ambaton Safina. Ya kuma san cewa shi Mustapha ɗin yayan Safina ne uwa daya uba daya. It cannot be a coincidence ace wannan yarinyar sunan ta Safina sannan kuma tana da yaya Mustapha. Ya san idan ya tabbatar wa da Mama cewa Safina yar uwar Safiyya ce to tabbas zasu yarda a fasa auren, ko ba dan komai ba ya san yanzu babu halittar da suka tsana irin Safiyya. Ya juyo da kansa, fuskarsa still dauke da murmushi, Al'ameen da yake ta kallon sa ya yi masa alamar tambaya "what?" Dan ya san ba da irin wannan fuskar suka taho ba. Amma Gidado bai kula shi ba so yake yi suje gidan ayi maganar a gaban Safina a gaban kuma Al'ameen yadda Al'ameen din zai zamo masa shaida a gurin iyayensa. Dan yanzu duk wani abun da ya shafi Safiyya ba yarda suke yi da maganar sa ba. Basu yi nisa sosai ba suka sauka daga kan titi suka shiga wani layi sannan suka shiga wani gida. Gidado ya bude ya fito yana kallon gidan, gida ne na masu rufin asiri, not luxuriously rich but middle class rich. Daga gani kuma gida ne mai mutane da yawa a cikin sa. Wadanda suka kawo su suka yi musu jagora zuwa bayan gidan, sannan suka shigar da su wani ƙaramin parlor. Suna fita Al'ameen ya tambayi Gidado "what? Menene kake ta fara'a haka? Don't tell me daga ganin yayanta har ka matsu da ka ganta" ya karasa cikin tsokana "Gidado ya zauna ya dora kafa daya akan dayar yana jujjuya ta yace "yes, in a way zaka iya kiran abinda nake ji a raina haka. Kai dai ka jira. You will be surprised with the outcome of this visit" Al'ameen ya zauna, trying as much as he can to be comfortable akan kujerar yace "to Allah ya sa muji alkhairi". Basu dade da zama ba wasu samari suka shigo su biyu suka fara jera musu kayan ciye ciye bayan sun gaishe su. Gidado ya yi tilting kansa yana kallon yaran kokari yake lallai sai yaga kamannin Safiyya a tare da su, sai da suka gama sannan yace "are you guys twins?" Suka juyo suna kallon sa sannan suka kalli junan su suka yi dariya. "no" daya yace dayan kuma yace "a'a. Abokina ne wannan. Dan makotan mu ne". Gidado ya koma ya jingina kansa a jikin kujera tare da rufe idonsa, yana jin al'ameen ya bawa yaran wani abu suka yi masa godiya suka fita. Sai da suka fita Al'ameen yace "kannen ta ne twins din da kake nema?" Bai bude idon ba yace "kannen Safiyya ne" Al'ameen yayi ajiyar zuciya yace "Gidado, gidan su Safina muka zo nan ba Safiyya ba. What is wrong with you" gidado ya gyara zama yace "na sani, akwai abinda nake tunani. You will understand idan ta fito. Ba'a jima ba kuwa ta fito ɗin. Kamshin turaren ta ne ya fara iso musu kafin ta karaso. Kyakkyawace son kowa kin wanda ya rasa. Fara tas mai cikar jiki da shape mai kyau wanda ta tabbatar ya fito a cikin doguwar rigar lace ɗin da ta saka, ba irin fitowar da za'a kira da tsiraici ba amma irin fitowar da zai dauki hankalin duk wanda ya kalle ta. Fuskarta da kwalliya dai dai gwardado. Tayi daurin dankwalin da ya zauna ɗas a kanta ya kuma bayyanar da yalwataccen gashin kanta ta baya. Ta yafa mayafi a side daya ya rufe rabin kirjinta. Ta tsaya a bakin kofa tayi sallama. Suka amsa mata a tare sannan ta shigo kanta a kasa ta zauna a kujera ta gaishe su "sannun ku da zuwa. Da fatan hanya bata gajiyar da ku sosai ba" duk suka yi shiru babu wanda ya amsa. Kowa yana saka ran dayan zai amsa. Sai kuma suka kalli juna a tare suka amsa "lafiya lau" "yauwa". Suka sake yin shiru gabaki daya. Ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da fingers dinta, Gidado kuma ya tsare ta da ido a ransa yana son ya ga ko zai iya tuno kamannin Safinar Safiyya, maybe ko ya taba ganin ta a hoto amma ya manta, yayin da shi kuma Al'ameen yake kallon Gidado da mamakin kallon da yaga yana yiwa Safina. Al'ameen ne ya katse shirun ta hanyar yin gyaran murya tare da cewa "malama Safina ya shirye shirye?" Ya fada already feeling awkward, dan shi ba gwanin magana bane ba musamman ga wadanda bai sani ba. Ta dago ido suka hada ido da Gidado, tayi murmushi tare da sake mayar da idonta kasa sannan tace "alhamdulillah. Ya naku?" Kafin ya amsa mata Gidado yace "ina twins?" Ta sake dago ido tana kallon shi, shi kuma yayi kokarin studying fuskarta yana neman yanayin mamaki amma sai yaga confusion. "Twins kuma? Wadanne twins?" Yace "naga Mustapha shi ya dauko mu dazu, na dauka tare da twins suka zo" ta sake bata fuska tare da girgiza kai "still ban gane abinda kake nufi ba. Mustapha daga ina yazo? Ai dama yana nan. But ka san shine wai?" Yace "shi Mustaphan ba yayan ki bane ba?" Ta gyada kai still cikin nuna rashin fahimta tace "eh yaya na ne, dan kanin baban mu ne. Ka san shi ne?" Gidado ya mayar da kansa baya tare da rufe idonsa, yana jin dutsen da ya daga daga kan zuciyarsa dazu yana komawa yana cigaba da danne ta. Al'ameen yayi saurin cewa "kamar naga kin kawo mana snacks, ɗan zuba min" ta mike da sauri ta dauki dan karamin plate ta na zuba masa samosa amma hankalin ta yana kan Gidado, ta durkusa ta mika wa Al'ameen still tana kallon Gidado tace "is he okay? Ko baya jin dadi?" Al'ameen yace "fine, he is fine, akwai serviette ne?" Ta dudduba gefe sai ta mike tace "bara in kawo". Tana fita Al'ameen ya ajiye plate din da ta bashi ya taba kafadar Gidado yace "kai lafiyar ka kuwa? What are you doing. What is with wani Mustapha and twins" Gidado ya bude idonsa, duk annurin da ya sauka a fuskarsa dazu ya kauce yanzu, yace "Piya tana da step sister mai suna Safina, and a step brother mai suna Mustapha. When I saw that guy yace min shi yayan wannan Safinar ne kuma sunan sa Mustapha, I thought......" Al'ameen yace "Muhammad! Must you relate everything to her? Komai na rayuwa sai ka jingina da ita sannan zai baka ma'ana. Are You telling me kazo gurin yarinyar da zaka aura and the first thing da kake kokarin tambayar ta shine ko ta san dangin tsohuwar budurwar ka? Does that even makes sense to you?" Gidado ya dauki robar ruwa ya bude ya daga ya shanye gabaki daya sannan ya ajiye robar. Yayi murmushin takaici yace "maybe I am loosing my mind. But yes. To me everything relates to her. Nothing makes sense to me in dai ba'a haɗa da ita a ciki ba" Al'ameen yace "then I don't think you are fit to marry " Gidado yace "ha! Finally someone ya fahimta. Go and tell that to Abba and Mama watakila su ma su fahimta" A dai dai nan Safina ta dawo hannunta rike da sabuwar serviette. Ta ajiye a gaban Al'ameen amma shi kuma sai ya mike. Tace "ba ka ci samosar ba" ya kalli samosar, shi ya manta ma ta ajiye masa, yace "thank you, zan dan je waje ne inyi waya" yana fita ta zauna akan kujerar da ya tashi daga kai tana kallon Gidado cike da damuwa tace "Habibi, kamar ba ka jin dadi ko? Ko tafiyar ce ta gajiyar da kai?" Ya dan juyo ya kalle ta "am fine. Kar ki damu. Yanzu zamu ga su baban? Gwara mu gama mu zo mu tafi" Ta dan bata rai "tafiya fa ka ambata, yanzu fa kuka zo and ko gaisawa bamu yi ba sosai musamman tunda yau muka fara haduwa. Ya kamata mu danyi hira ai ko?" Ta karasa tana langwabe kai gefe. Ya gyara zamasa yana kallon ta yace "hira? Okay what do you want us to talk about?" Tace "at least ka fada min ya ka ganni? Tunda yau ka fara ganina. Gwara in san cewa nayi maka ko ban yi maka ba. And maybe tell me abinda yake damunka, watakila ina da maganin sa" yace "does that really matter? Kina ganin ra'ayi na akan ki yana da muhimmanci?" Ta mike ta ta bi ta gabansa zuwa inda kayan abincin suke ta zubo masa juice ta hado da snacks a plate ta dawo inda yake ta durkusa a gabansa ta mika masa juice din sannan ta koma ta zauna ta dora snacks din akan cinyarta tace "ra'ayin ka a yanzu shine yafi komai muhimmanci, musamman ni a gurina. Abinda kake so shine abinda zan saka a gaba na, abinda ba ka so shine abinda zan fi ki fiye da komai" yace "tell that to my parents" ya kurbi juice din ya ajiye yace "send me your account details, zan turo miki kuɗin da zaki yi hidima, am sure kina shirya wani abu da kike so kiyi. And if you need anything, message me". Ranta ya baci har fuskarta ta nuna, tace "yanzu dai ba zanji cewa nayi maka ko banyi maka din ba? Duk wannan kwalliyar da nayi?" Ya mike tsaye "ban boye miki komai ba Safina. And you agree to take your chance with me. Wannan shine dai dai lokacin da zaki fara hakurin da kika yi alkawarin zaki yi" ta mike ita ma "kayi hakuri. Kar ka bata rai dan Allah. Kawai dai kasan mu mata muna da son yabawa, and when I walked in I noticed kana ta kallona, I thought na samu wani bangare na zuciyar ka" ya juya yayi hanyar fita, har ya kai bakin kofa sannan ya juyo yace mata "I was looking at you because I thought you were someone else, it turned out ba ita ce". Sai ya juya ya fita. A waje ya hango Al'ameen yana waya, ya tafi gurinsa ya tsaya har ya gama, ya fahimci cewa da matarsa Humaira (read *Aisha Humaira*) yake magana saboda yadda yake ta zabga murmushi shi kadai, love is truly the most beautiful feeling ever. Sai da ya gama sannan ya juyo yana kallon Gidado yace "wai fitowa kayi ka bar ta ita kadai?" Yace "kai ma ba fitowa kayi ka bar ni ni kadai da ita ba?" Al'ameen ya danyi dariya "guri fa na baku ku gaisa sosai" Gidado yayo dan karamin tsaki "I can't stay inside with her. It is suffocating". Haka suka cigaba da tsaiwa a waje duk su biyun, har sai da Mustaphan da ya dauko su dazu yazo yayi musu magana sannan suka koma ciki tare, basu tarar da ita ba. Ya zauna ya saka su a gaba sai da suka dan ci abinci kadan sannan ya nuna musu toilet suma yi alwala suka zo suka yi sallah, daga nan kuma ya fita sai gashi sun dawo tare da manya su biyu, wadanda duk suka baiyana wa su Gidado kansu a matsayin wan baban Safina da kuma kanin sa, suka tabbatar musu da cewa suna goyon bayan auren suka kuma bawa Gidado assurance ɗin cewa ba zai samu matsala da Safina ba. "Tun tana jaririya mahaifinta ya rasu. Ni na rike ta tamkar ni na haife ta, ko bayan aure gurin na zaka zo akan duk wata bukata, kar ka yarda wani daga baya ya fito yazo yace maka shine yake da iko a kanta. Mune dangin ubanta mune komai nata" Babban cikin su ya faɗa. Da zasu tashi Al'ameen ya ajiye musu kudi masu kauri yace su sayi turare Sai da zasu tafi sannan Gidado ya tuna da sakon ta da Mama ta bashi ya kawo mata, ya mika wa Mustaphan da yake tare da su yace ya kai mata, yayi dariya "kai dai kawai kace inje in kira maka ita kuyi sallama" ya kira wata yarinya "je ki cewa Safina tazo angonta yaƙi tafiya yace sai ya ganta". Ba'a jima ba ta fito, ta yafa mayafi sosai wannan karon ta rufe jikinta. Gidado ya mika mata ledar hannunsa "inji Mama" ta karba tana murmushi "Nagode sosai. Zan kira ta inyi mata godiya" yace "good. Mu zamu tafi. Ki turo min sakon da nayi miki magana a kansa" ta girgiza kai "no ka barshi kawai. I already made plans" ya daga kafada "okay. Alright" har ya juya ssi kuma ya dawo "I just heard cewa babanki ya rasu, you never tell me" ta daga kafada itama "you never ask" yace "maman ki kuma fa?" Tace "tana Abuja. Da ya rasu ta koma gurin sister ɗin ta a Abuja. Yanzu ma tana can. A can zan sauka lokacin bikin. A can zata yi nata taron" ya gyada kai. "Okay. Alright. Am sorry for your lost. Allah yaji kansa" ta langwabe kai "Ameen. Na kusa daina maraici ai. Insha Allah. Am sure mijina zai kula da ni sosai". Har suka je airport basu yi magana da junan su ba, har jirgin su ya tashi ya kuma sauka a Abuja basu tattauna akan komai ba. Gidado was consumed in his thoughts yayin da shi kuma Al'ameen ɗin ya rabu dashi dan ya fahimci baya cikin mood din maganar. Sai da suka sauka suka shiga mota zasu je gida sannan Gidado yayi wa Al'ameen magana "Ya Ameen, please tell me the truth, do you think I am loosing my mind and imagining things?" Al'ameen ya rage gudun da yake yi yace "i don't think you are loosing your mind. But I believe you are overthinking everything" Gidado yace "then advise me? How can I stop thinking? How can I stop thinking about her?" Al'ameen yace "I am not expert in this thing, amma ina ganin you need to get something that will keep you busy, wani abu da zai dauke maka hankalin ka daga tunani, maybe shine dalilin su Abba na yi maka aure thinking matar zata dauke maka hankalin ka, but I advise ka samu wani abu ka dinga yi, ka daina zama kai kadai, ka gajiyar da jikin ka da ƙwaƙwalwar ka yadda ko dare ne yayi kana kwanciya zaka yi bacci. Sannan get rid of anything da zai ke tuna maka da waccan yarinyar" Gidado ya danyi murmushi yace "I tried doing that. But she is everywhere. Har cikin bacci na take shiga. I always dream about gani na da ita na karshe. And the more I saw her a cikin mafarkin the more I feel the need to get back to her. Gani nake kamar kokarin mantawa da ita da nake yi yanzu ba dai dai bane ba. Gani nake kamar nayi betraying dinta, she needed me and I shut the door on her face" Al'ameen ya tsayar da motar ya juyo sosai yana kallon sa "I can't believe this. You betrayed her fa kace? How? I thought ita ce ta yaudare ka ta saka kuka yi soyayya alhalin tana da aure? Ko kayi bincike ne ka ga cewa bata da auren karya take yi?" Gidado yace "she is married. Wannan bani da shakku akan sa a yanzu. But ....." Al'ameen ya bude hannu yace "but what Muhammad? She is married and pregnant for her husband. Kai kace min kaga cikin da idonka. For God's sake stop creating things in your head and blaming yourself alhalin kai ne victim din" Gidado ya dago kai yana kallon Al'ameen da wani irin kallo yace "ranar da tazo gurina na karshe, ranar da ta gaya min cewa tana da aure. She looked broken, sad, and devastated. She looked like a shell of her former self. Akwai wani abu da ya faru da ita, wani abu da ya mayar da ita haka. Ba haka take ba. She was the most cheerful person I have ever seen. And sanda na kore ta daga office ɗin, ta tsaya a bakin kofa ta miko min hannu and called my name, kamar tana neman taimako daga gare ni, but i did not listen. I shut the door. And now duk sanda na rufe ido na scene din da nake gani kenan. Har cikin bacci na nake jin tana kiran sunana" Al'ameen ya dafe kansa tare da rufe idonsa, Gidado yace "you really think I am loosing my mind, right " Al'ameen ya bude idonsa yana kallon Gidado yace "no. I think you love that girl too much, and I think you need to see a therapist, you need to see Mammy". Gidan su Gidado suka fara zuwa, suka yi packing Gidado ya bude kofa ya fita sai kuma ya dawo ya zauna yana kallon Al'ameen yace "one more question, ka taba ganin Safiyya, do you think she loved me ko kana ganin tun a lokacin she was playing me?" Gidado yace "guy! Anya kuwa kana kallon kan ka a madubi, anya ka fahimci irin haduwar da kayi? Bana jin a duniya da akwai wata ya mace mai jini a jika da zaka ce kana so kuma ya kasance bata son ka. Tabbas a lokacin da na ganku da Safiyya tana son ka. But that doesn't matter now. Don't tell that matter". Gidado yayi murmushi fuskarsa tana nuna jin daɗin maganar yace "thank you ɗan uwa, I really appreciate this". Forgive the typos please Dan Allah kar kuce yayi kaɗan 😅🤫 Littafin Safiyya is 500 naira via 0779484494 Nafisa Tafida Usman Access Bank Send the evidence via telegram or WhatsApp to 0704 203 0419 Posting of paid episodes will be on telegram only. Dan Allah idan da akwai wadda ta turo evidence dinta ban saka ta a group ba should talk to me so that your message will come up. Nagode sosai. I really appreciate all the love. [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤‍🩹*Safiyya*❤‍🩹 *By* *Maman Maama* *Episode Thirteen: One Day Apart* Free Episode Littafin Safiyya is 500 naira via 0779484494 Nafisa Tafida Usman Access Bank Send the evidence via telegram or WhatsApp to 0704 203 0419 Posting of paid episodes will be on telegram only. Kwana biyu bayan zuwan su Katsina, Gidado ya saka Safina ta turo masa address ɗin matar da aka ce yaje ya gaisar anan Abuja, sunan ta Hajiya, kuma kamar yadda Safina ta gaya masa mahaifiyar ta ma tana tare da Hajiyar a lokacin. Dan haka ya shirya ya ɗauki Haidar suka tafi tare. Tun daga gate ɗin shiga gidan suka fahimci cewa wannan gidan masu kuɗi ne, real kuɗi, tsohon kudi. A bakin gate mai gadi ya tambaye su gurin wanda suka zo, Gidado yace "Hajiya, ina fatan tana nan ai ko. Am sure ta san da zuwan mu" maigadin yayi murmushi yace "ko sirikin na mu ne? Tun safe Hajiya tace zata yi bako, tace mai neman auren Safina ne zai zo, ai Mommyn Safina ma tana gidan. Allah ya sanya alkhairi ya sa da mu za'a yi" Gidado ya danyi shiru yana kallon sa, babba ne sosai kuma daga ganin sa kasan ya san jiya ya kuma san yau, irin masu aikin gidan nan da suka zama yan gida. Sai yayi amfani da damar sa yayi kokarin sanin wani abu akan Safina. "ka san Safina kenan sosai" mai gadin yace "sosai ma. Safina ai kamar jika take a gidan nan. Mahaifiyar ta ma a gidan nan ta tashi tun tana karama har aka aurar da ita har yau kuma nan shine gida a gurin ta. Ai yayar mahaifiyar ta ce matar gidan nan. Kuma tunda ita ta rike ta sai ta zama kamar ƴa ce a gidan. Safina kuma kaga ta zama jika ce. Kai kuma ka zama sirikin mu. Allah dai ya sanya alkhairi" Gidado yayi murmushi "na kusa zama. Not yet. Nagode Baba. Ameen. Dan Allah a sanar musu mun zo" Mai gadin ya bude musu gate suka shiga da mota sannan ya kira wata yarinya da tazo wucewa yace ta je ta gaya wa Hajiya baƙin ta sun zo. "Saurayin safina ne?" Yarinyar ta tambaya cikin rada amma su Gidado sunji, mai gadin ya fara yi mata fada "maza ki tafi aiken da nayi miki, ku baku da aiki sai shegen tsegumi". Su Gidado suka fito daga motar a tare, Haidar ya zagayo side ɗin Gidado yace "tana nan ne?" Gidado ya kalle shi yace "wa?" Haidar yayi murmushi "ita ɗin dai" Gidado ya bata rai "zaka koma gida wallahi" Haidar yayi dariya "wai naga sai wani bobboye ta kake yi ne. I just want to see her in lissafa mata irin abubuwan da nake so da kuma wanda bana so. Kasan ana gama bikin ku can zan koma. Though ba Safiyya bace ba amma wancan alkawarin bai karye ba. Har na zaɓi daki ma" Gidado yace "tsakanin ku ne wannan, ni ina ruwa na?" Haidar yace "to ai baka haɗa ni da ita ba dan haka akwai ruwanka a ciki, dole kai zan bawa sako ka isar mata. Ina fatan ta iya girki, ina nufin girki irin five stars standard ɗin nan". Kafin Gidado ya bashi amsa aka yi musu magana aka ce su shiga. Suka jera suka tafi, sai Gidado ya samu kansa da murmushi yana tuno irin soyayyar da take tsakanin Safiyya da girki. She and Haidar would have been friends. She even promised him that. Ya tuna da wani lokaci da tayi wannan alkawarin. ****.     ****.     ****.     ****.     ****.    *** Waya suka yi da safe a muryarsa ta fahimci cewa he was stressed. Da ta tambaye shi dalili sai yayi mata complain cewa aiki ne yayi masa yawa a office, har zuwa rana ma da suka kara wayar still bai kammala aikin da yake yi ba. Da yamma sai gata ta baro hostel dinsu ta dauko motar ta tazo har office ɗin sa ta kira shi a waya tace ya fito ya ga wani abu. He complain cewa aiki yayi masa yawa amma shi kansa ya san cewa ba'a cewa Safiyya "no" dan yanzu sai ta saka masa kuka. Dole ya rufe office ya fito ya same ta a mota, ta bude masa gaba tace "get in" ya shiga yana kallon ta "what?" Tace "to ka rufe motar mana so kake mutanen da suke waje su ga abinda zan nuna maka. Sirri ne" yayi ajjiyar zuciya "Piya! Aiki nake yi wallahi. Dole a yau zan gama aikin nan kuma ko rabi ban yi ba. Ko kina so a kore ni ne?" Tace "waye zai kore ka? Abba ko uncle Habib? You own dis school. Oya, close the door" ya jawo kofar ya rufe "yes ma'am" sai kawai gani yayi ta saka mota a giya ta fara tafiya, ya bude ido "what are you doing Piya? Ina zaki kai ni?" Tace "I am kidnapping you, kuma sai an biya ni ransom zan dawo da kai". Ya gyara zaman sa yana kare mata kallo, abaya ce a jikinta da mayafin abayar a kanta. Fuskarta fes babu kwalliya, fatarta kamar kullum tana kyalli da daukan ido. Ta kalle shi ta gefen ido. "ka daina kallo na. Ko so kake inyi tuntube ne" yace "you are driving, not walking " tace "to in na buga motar fa?" Yace "tunda kin hana ni yin aiki na ba gwara in zauna inyi ta kallon ki ba, kar inyi biyu babu" tayi murmushi "believe me, you are going to enjoy this. Zaka gode Allah cewa I kidnapped you today" yace "zan rubuta a diary in ajiye wa yaran mu, in gaya musu maman su taje har office ɗina tayi man-napping ɗina" tayi dariyar kalmar da yayi amfani da ita a dai dai lokacin da suka zo gate din fita daga makarantar. Sai da suka fita yace "seriously, ina zaki kai mu ne wai?" Tace "park. You need a rest. I couldn't take jin ka a gajiye. It doesn't suit you" ya bude ido "baby ni namiji ne fa? Dole sai nayi aiki. In banyi ba da me zan kula da ke da yaran mu?". Sai da suka yi nisa sannan ya juya yana kallon seat din baya "wai abinci ne a bayan motar nan? Kamshi nake ji" tace "abinci ne mana. We are going to have a picnic. And I know ko lunch baka yi ba. Ya shafa cikin sa, ko breakfast din kirki bai yi ba kuma yanzu kamshin abincin ya kara masa jin yunwa. Ya juya yana kallon ta yace "you are amazing Piya. Thank you. Zan iya fara ci yanxu?" Ta girgiza kai da sauri "not in my car" ya daga hannu "nayi alkawari ba zan bata miki ba" and he knows he dare not. Dan muguwar tsafta ce da ita. A karshe dai haka ya hakura har suka je gurin. Shi yayi musu shinfida da abin shimfidar da tazo tashi, ita kuma ta jera musu abinci, sannan ta jera masa a plates ta ajiye masa a gabansa. Farko har zaiyi mata dariyar ta zuba masa da yawa, saboda shi ba mutum ne mai cin abinci sosai ba, amma yana ci tana bashi labarin dramar da ake a hostel dinsu bai san sanda ya cinye ba sai gani yayi tana kara masa. Ya hadiye lomar bakinsa yana jin daɗin abincin yace "Piya, duk sanda aka yi bikin mu, ina jin Haidar gidan mu zai dawo da zama" tana kallon sa itama tace "saboda me kace haka?" Ya nuna plate din abincin gabansa yace "abinci, saboda kaunar da yake yi wa abinci. Saboda ke kuma kin iya abinci" tayi murmushi fuskarta tana nuna jin daɗin maganar sa tace "bayan bacci, the second thing da na iya a rayuwata shine girki. I can cook. Irin I can really cook" yace "banda yabon kai dai. In mutum ya iya abu ai bari yake yi mutane su yaba ba wai shi ya zauna yayi ta yabon kansa ba" tace "saboda me? Abeg let me brag about my achievement tunda bani da abubuwan bragging for da yawa. I can cook. Na iya girki wato nake gaya maka" yace "there is something else da kika iya kuma ai, wanda ya kamata a baki medal a kansa" ta gyara zamanta tace "what? Tell me please, in kara shi akan list of achievements ɗina a rayuwa" yace "crying. You can cry for Africa. Ni ban taba ganin ma mai saurin kuka irin ki ba". Tayi dariya "haha. Duk kuka na ai mai dalili nake yi, is either an hana ni yin abinda nake so ko kuma an takura min sai nayi abinda bana so. In ba'a so inyi kuka kawai a barni in yi abinda raina yake so" yace "ai na fahimci haka. Kuma na fahimci laifin Daddy ne. Shi ya shagwaba ki beyond repair. Ni yanzu an barni da sabon raino. In mun haihu ban san wa zan goya ba, ke ko yaran" ta bata fuska "wanda kafi so. A lokacin zan gane matsayi na ai" yayi murmushi yana cin burger din daya ajiye masa a gabansa da zafinta, duk kuwa da cewa jin cikinsa yake yi kamar zai fashe. Yace "wai in tambaye ki Piya, yanzu in muka haihu, in yaron yana yi miki kuka ya zakiyi da shi?" Tayi shiru tana tunani sannan tace "zama zanyi nima in yi masa kuka" ya ajiye burger din yana dariya sosai, sai da ya gama sannan yace "I can't wait for that time. You will look so cute with kids" tayi murmushin ta mai kyau tace "I can't wait either. I love kids. Ban san yadda ake musu ba saboda gidan mu babu yara but I will learn. I will be the best Mom ever". Sai da suka gama cin abincin sannan ya kira Haidar a waya. "albishirin ka. Ka kusa barin gidan Abba. Dan na tabbatar duk sa da akayi bikin mu da Safiyya gida na zaka koma" Haidar yace "saboda me?" Gidado yace "saboda ta iya girki. Kuma tana kaunar girki. She will just keep feeding you har sai ka kasa tashi. Nima abinda ya faru da ni kenan yanzu" sai kuma ya mika wa Safiyya wayar "gashi yace in baki" ta bude ido tana girgiza kai "in kuma suna tare da Mama ko Baba fa? Ai sai suce bani da kunya" yace "shi kadai ne fa" tace "to in ya basu labari fa? In yace musu munyi waya fa?" Gidado yayi ajjiyar zuciya "ba zai fada ba, zan gaya masa kar ya fada" ta langwabe kai "kayi alkawari?" Yace "yes, nayi alkawari" sai ta karbi wayar ta saka a kunnen ta, taji muryar Haidar yana dariya yace "nima nayi alkawari" sai taji kunya ta rufe fuskarta kamar yana gurin. Suka gaisa, yana ta tsokanar ta, sannan a karshe tayi masa alkawari "ka kusa dawowa gidan yayanka da zama. Kai zaka fara zabar daki a gidan. Abinci kuma sai wanda ka zaba za'a ke girkawa a gidan". Sai da suka gama wayar ta mikawa Gidado sannan taga ashe shi kallon ta yake tayi, ta sunkuyar da kai tana jin kunya yace "you know what? I am glad you kidnapped me. And I am looking forward to you kidnapping me again. I get to look at you instead of papers. ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    ****.    Suna shiga cikin gidan wani katon parlor aka kai su. Suka zauna aka fara hidimar kawo musu fruits da snacks da drinks iri iri. Haidar zai fara ci Gidado ya harare shi sai ya koma ya zauna yana bata fuska. Basu jima ba wata dattijuwar mata ta fito tare da wata yar budurwa, yarinyar ta taimaka mata ta zauna a kasa sai su Gidado suma duk suka sauko suka zauna a kasan. Tace "bana iya zama kan kujera yanzu, ciwon kafa ya sako ni a gaba. Kun san jikin tsufa. Ko da yake ku ba zaku fahimta ba". Suka yi murmushi sannan suka gaishe ta a tare, ta amsa musu da sakin fuska sosai tare da tambayar su mutan gida. Ta nuna Gidado tace "na gane mai gidan nawa, waccan marar kunyar ai takanas ta aiko min da hotonsa ta waya wai ta samu mijin xa yafi nawa kyau, ni kuwa na san ko a yanzu kuka jera kai da Alhaji sai yammata sun dauki Alhaji sun barka" ta karasa maganar tana dariya. Suma suka yi murmushi. Ta cigaba "naji daɗin zuwa da kayi ka gaishe ni, hakan yana nufin ka girmama ni kenan. Ina kuma so ka dauke ni tamkar uwa ba ma kaka ba, ni uwar kowa ce. Ni ka ganni nan Allah bai bani haihuwa ba amma kuma yayi min baiwar mutane. Wannan ya sa gashi dai shekarun girma sun zo min amma bana kukan rashin yaya, yaran da na rike sun zama gata na. Yayan yanuwana da na mijina duk dauka nake yi in rike su kamar ni na haife su, sannan kuma in debo marayu in rike su suma in basu duk kulawar da ya dace iyaye su bawa yaya, ko yan aiki aka kawo min na lura basu da cikakken gata a gidajen su sai in mayar da su yayana in rike su har in aurar da su. Ba zan iya lissafa yan aikin da na rike ba, tun daga kan Safiya har zuwa wannan yarinyar ta gaba na Lubabatu. Allah sarki Safiya Allah ya kai rahama kabarin ta. Duk da bata raye amma har yanzu ina morar gatan da na yi mata". Su Gidado suka ce "Ameen" ta cigaba "ina gaya maka wannan ne dan ka saki jikin ka, nan gidan mutane ne, kowa kuma namu ne ballantana kai da aure zai hada mu. Ka fahimta ai ko?" Gidado yayi gyaran murya yace "na gane. Na gode kuma sosai. Allah ya kara lafiya" tace "Ameen ya Rabbi. Ai an gaya min cewa kai jika ne a gurin marigayi ambassador Muhammad Dikko. Mutumin kirki. Allah ya kai rahama kabarin sa. Na san shi ai lokacin da yana da rai, na kuma san matarsa Hajiya Fatima, ban sani ba ko zata gane ni amma in kaje kace mata Hajiya Maryama matar Alhaji Nasiru Atafi tana gaishe ta" Gidado yace "insha Allah za'a gaya mata". A lokacin wata mata ta sauko daga sama, kallo daya Gidado yayi mata ya fahimci cewa ita ta haifi Safina, kamar su daya sai dai safina zata fi ta farar fata sannan da kuma bambancin shekaru. Ta zauna akan kujera a gefen su Gidado, suka juya suka gaishe ta ta amsa musu babu yabo babu fallasa sannan tace "sai yau ka samu damar zuwa gaishe mu kenan". Hajiya tace "menene haka Sa'adatu? Tunda yazo ba shikenan ba?" Tace "ni kinsan bana barin magana a ciki na. Amma muna gari daya ace sai few days to auren Safina sannan zamu ga mijin da zata aura? A hakan ma kuma sai da nayi waya nayi wa mahaifiyar sa korafi sannan yazo, da bai yi niyyar zuwa ba ai. Da sai dai ranar bikin muma mubi cikin mutane muna tambayar ina angon yake" Hajiya tace "tunda dai ita amaryar ta san shi ba shikenan ba?" Sai kuma ta juya gurin Gidado tace "rabu da ita, ita in dai idonta ya ga abu sai bakin ta yayi magana, haka halinta yake, zaka saba da ita a hankali. Tana da kirki sosai sai dai zaka sha faɗa" Mommy tana daga gefe ta kuma cewa "an anyi abu ba dai dai bane ba ai nake yin fadan" Hajiya ta chanza maganar ta hanyar yi musu korafin ba su ci komai da aka kawo musu ba, su kuma suka bada uzurin cewa sunci abinci a gida kafin su fito. Amma duk da haka sai ta saka aka kwashe komai da aka kawo musu aka kai musu mota. Da haka suka yi musu sallama suka tafi. Suna shiga mota tun kafin su bar gidan Haidar yace "I don't like wannan surikar taka" Gidado yace "that makes the two of us" bayan sun dauki hanya kuma sai Haidar ya fara dariya yace "ka san tunanin da nayi, ina ma ace tare da Aunty Hafsat muka je gidan nan matar nan tayi mana wannan mulkin" Gidado yayi murmushi yace "da anyi yaki kuwa. She will humble her. Zan so inga yadda zasu kare da bikin nan". *Her* 🧕🏻 Kwanaki suna ta tafiya har ya rage saura sati biyu lokacin da likita ya saka za'a yi min aiki yayi, amma sai naji sam bana jin tsoron aikin da za'a yi min ban damu da cewa wai cikina za'a yanka a fito da ɗan mutum ba, ni dai kawai burina shine in rabu da mayataccen cikin nan ko na samu in shaki iska mai daɗi, ko na samu in dai na ganin disappointment a fuskar Daddy a duk lokacin da ya kalle ni, ko na samu in manta da abinda ya same ni. Sai dai ni kaina na san cewa rabuwa da cikin ba zata taba goge abinda ya faru daga zuciya ta ba, babu abinda zai fari da zai saka in manta da abinda aka yi min. Zalincin da aka yi min. Babu kuma abinda zai saka in yafe wa wanda yayi min. Har abada. A lissafin Daddy naji yace aiki na zai kama washegarin daurin auren Safina. Ni kam ban ma rike date din da aka saka na auren Safina ba. Dan ni ba ma na gane ranaku a yanzu. Akwai kawayen mu da yawa da suke ta yi min magana a chats akan bikin Safina, ni kuma na kan basu amsa da cewa nayi tafiya jinyar Daddy dan haka bana nan za'a yi. Safina kam sai shirye shiryen ta take yi. Ta kan turo min pictures na kaya tace in taya ta zaba, har kayan da zata saka na kowanne event da zasu yi sai da ta turo min, sometimes na kan yi ignoring dinta dan ni abinda yake gaba na yafi karfin zaban kayan sawa, sometimes kuma sai in bata amsa dan kar ta ga kamar dan nasan kudin indirectly daga gurina zasu fito shi yasa na ke wulakanta ta. Kamar yadda nayi tunani, su yan uwan nata da ta tafi Katsina gurin su dan suyi mata aure babu abinda suka yi mata na kayan daki, haka a dole Mommy ta sauko daga fushin da tayi da Daddy ta dame shi da waya akan ya bada kuɗin da za'a yi wa Safina kayan daki, direct yace mata bashi da kuɗi, besides, ai tace masa Safina ba yar sa bace ba. Sai ta koma gurin Uncle Ahmad shi kuma yace mata ta tambaye ni amma sai ta kasa tambayar tawa ta cigaba da bin Daddy, har sai da Daddy ya tabbatar tayi laushi sannan yace da Uncle Ahmad ya bata. Haka suka yiwa uncle Ahmad bill tun daga kan kayan daki har zuwa kayan da zasu saka na fitar biki, shi kuma ya raba biyu ya basu rabi yace ba zai bayar ga baki daya ba. A lokacin ne Safina ta yi min dogon message akan maganar, wai uncle Ahmad zai saka suji kunya, wai tun yanzu ya fara nuna musu cewa su ba yanuwan mu bane ba, dan Allah inyi masa magana. Banyi masa magana ba sai na yiwa Daddy magana, tunda na fahimci shi sulhu yake so yayi a tsakanin mu shi kuma uncle Ahmad so yake a raba gari kowa ya kama gabansa. A ƙarshe dai Daddy ya saka Uncle Ahmad ya cika musu kuɗin suka yi duk siyayyar su suka gama. A ranar da yake saura sati daya aikina, na tashi da safe kamar yadda na saba na shiga kitchen na haɗa smoothie na sha sannan na shiryawa Daddy breakfast. Na dauka na kai masa dakinsa na tarar yana kwance idonsa a rufe amma daga gani na gane ba bacci yake yi ba. Na jawo table gabansa na dora abincin na zauna a gefe nace "Daddy ga breakfast. Ka tashi ka ci". Ya tashi zaune da kyar, na lura da effort din da ya saka yanzu gurin tashin yafi yadda yake yi da, ciwonsa yana kara cigaba a kwanakin nan fiye da yadda yake da. Ya zauna ya debi oats din dana dama masa a hankali ya kai bakin sa, na kara lura da yadda hannunsa yake rawa sannan da kuma yadda ya hadiye abincin da kyar. Ya lura da kallon da nake yi masa yayi gyaran murya yace cikin muryar da ta kara zama weak "doctor yace nan da wata uku, that's idan na kai nan da wata uku, I will be needing a feeding tube, ba zan iya cigaba da hadiye abinci da kai na ba. Kin gane?" na gyada kai na da sauri tare da sunkuyar da kaina ina kallon ciki na da yanzu baya boyuwa a cikin riga ta. Ya kira sunana "Safiyya" na dago kai na kalle shi yace min "don't cry" na sake sunkuyar da kaina ina jin hawaye na suna zuba kan cinyata. Nayi saurin goge su. Sai ya sake kiran sunana "Safiyya" na dago kai, yace "munyi magana da Ahmad, za'a daura auren ki da Mukhtar washegarin da akayi na Safina, in anyi miki aiki da safe, da yamma za'a daura miki aure. Saboda baƙin da zasu zo na Safina ba sai sun koma ba sai a daura naki. Do you understand?" Na sake gyada kaina ina rike hawayena. Sai na mike na yi hanyar fita, har na kai kofa ya sake kiran sunana "Safiyya " na juyo yace "kin fahimci dalilin yin auren nan ko?" Na sake gyada kaina ban ce komai ba na fita da sauri. Daki na na wuce da sauri na rufe kofa sannan na zube a kan carpet din gaban gadon dakin na fara rera kuka. Kukan abubuwa da yawa. Kukan da ban san ranar da zan daina shi ba [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: Daki na na wuce da sauri na rufe kofa sannan na zube a kan carpet din gaban gadon dakin na fara rera kuka. Kukan abubuwa da yawa. Kukan da ban san ranar da zan daina shi ba alamar an bude kofar dakin an shigo, ban dago kai na ba amma a raina na san waye saboda mu biyu ne kadai a cikin gidan, besides, motsin wheelchair dinsa daban yake da motsin tafiyar sauran mutane. Ban juya na kalle shi ba amma nayi kokarin sassauta kuka na tare kuma da kokarin goge goge hawaye na. Ya jima anan a zaune yana kallo na sannan yace "I knew it. Dana na san kina nan kina kuka. But what I do not know is kukan menene kike yi? Uhmm, fada min, kukan me kike yi". Na cigaba da goge fuskata da bayan hannun rigata, ina jin yadda already fatar idon ta kumbura. Ya sake tambaya, "ina jin ki? Kukan menene kike yi?" Nace "I want you to get better. I need you to get better" yayi shiru na wani lokaci sannan yace "you know it is not going to happen. Sai kuma menene again?" Na girgiza kaina "shikenan dama. Shine kadai abinda nake yi wa kukan" yace "liar. You are also crying saboda maganar auren ki. Haka ne?" nayi shiru banyi magana ba. Ya sake tambaya ta "ba kya son auren Mukhtar? Kina so a fasa yi da shi?" Nayi shiru still ban ce komai ba. Ya zagayo kujerar sa gaba na yace "Safiyya. Ina so inyi miki aure kafin in tafi in barki. Idan na mutu na barki babu miji this people will tear you apart. Kuma dole in aura miki wanda ba za'a yi bincike ba ballantana a tono abinda ya faru da ke. Wannan ya bar ni da very limited da ke. Wannan ya bar ni da very limited options. I gave you the options. And you chose. Wanda kika zaba ba shi zuciya ta take so ba, hi zuciya ta tafi yarda da ki auri Mustapha. But you adamantly chose Mukhtar. And now you are crying. Tell me why". Na dago ido na ina kalion sa "Daddy, me yasa kake son Mustapha?" Yace "saboda a hannuna ya tashi, ni na bashi tarbiyya. Saboda mahaifiyarsa ce ta raine ki, ita ta baki tarbiyya. And sometimes family means more than blood. Sa'adatu will never harm you. But I am not so sure about Ahmad" Na dauke kaina gefe nace "you know what they want" yace "and what makes you think cewa su Ahmad ba the same thing suke so ba?" Nayi shiru ban ba shi amsa ba sai ya sake cewa "a rayuwa Safiyya, most of the relationships if not all da zaki shiga, ko ta auratayya ko business ko zamantakewa to trade by batter ake yi, to get something you have to give something. The best logic is ki san abinda mutum yake so daga gare ki, and then use that to get kema abinda kike so" Nace "Amma Daddy Mustapha fa..." Yace "he didn't do it. Ban san how many times zan gaya miki ba. He didn't do it" nayi shiru ban ce komai ba, bana son gaya wa Daddy abinda Mustapha yayi, bana son inyi using the only card din da nake amfani da shi grin taming Mustapha. Jin nayi shiru bance komai ba sai yace "are Jin nayi shiru bance komai ba sai yace "are you changing your mind or not?" Na goge hawaye na tare da girgiza kaina "no. Am not. Ina neman alfarma dai guda daya. Dan Allah Daddy bana son komawa Nigeria. I want to live here. Or somewhere else. Anywhere that is not Nigeria",. Ya juyo yana kallona, sai kuma ya juya kujerar sa yayi hanyar fita ba tare da yace min komai ba. Har ya kai bakin kofa sannan ya juyo yace min "about Mukhtar, ko da ana gobe daurin aure ne in kika chanja shawara let me know ni kuma zan tsayar da maganar". Ban amsa ba nima har ya fita, ban kuma bar space a zuciya ta da zan yi tunani akan maganar ba. Na riga na yanke shawara and I am not going back on it, duk kuwa da zafin da zuciya ta take yi min akan hakan. Yana fita waya ta ta kama kida, na san waye tun kafin ma in kalle ta dan mostly ya kan kira ni by this time. Sai dai sam bana son daukan wayar ta sa. Zuciya ta bata so. Sai nayi murmushi ina mamakin rayuwa ta, yanzu na gama ja in ja da Daddy a kan sa, akan nace shi zan aura, amma kuma still zuciyar ba son sa take yi ba. 4 8:00 PM Har ta katse ban dauka ba sai da ya sake kira sannan na dauka. Na saka wayar a kunne na banyi magana ba yace "ko baccin ne dai? Na ga alamar ke ba kya gajiya da bacci" nace "na tashi, kawai dai yau na tashi bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin dadi na tashi. Have you heard the good news? In the next eight days you are going to be my bride. Duk da dai su Daddy suna ta insisting babu taron biki, but I want us to have ko da yar walima ne haka in kin dawo nija... .." Nace "yaya Mukhtar, I am sorry, but I don't want any walima dan Allah. And I also don't think zan dawo Nigeria." Yace "why not? Fiyya komai da ya faru ai ya wuce kuma. Daga anyi daurin auren nan shi kenan we will put everything behind us muyi facing sabuwar rayuwar mu and the ways to build a new family k0? Gashi ma Allah cikin ikonsa we will soon have a child to start the family with. Abeg, ki shafa min kansa ko kanta and tell them they are already loved at home". Abinda ya fada was supposed to made me feel better amma sai naji raina ya baci dan a lokacin bayan uban dan cikina babu abinda na tsana sama da dan cikin nawa. Amma sai na daure zuciya ta nace "kayi hakuri yaya Mukhtar. I can't. Abun zai wuce physically, but the trauma will always haunt me, and the best thing to do idan mutum yana son moving on from a traumatic experience is to change environment. Idan na dawo Nigeria ba zan iya bawa family na kulawar da suke bukata daga gare ni ba" yace "kina ganin zaki ke tunawa da shine?" Nace "not just him, Zan ke tunawa da komai" amma a raina na san babban abinda nake gudu a komawa Nigeria shine Muhammad. A yanzu da na dan saka distance a tsakanin mu gani nake kamar na samu wata kariya daga ciwon son kamar na samu wata kariya daga ciwon son sa, amma ina komawa Nigeria na san zanji tamkar an rushe katangar kariyar ne, and there is a chance na cewa zamu iya haduwa da shi, and that would be a disaster. A haka dai ya hakura ya bar ni amma bai ce ya amince ba kamar yadda Daddy ma bai ce ya amince ba, ya dai ce min zaiyi tunani a kai. Daga ranar sai na kara cigaba da lissafi na. Ina lissafa ranar aiki na kuma ina lissafa ranar daurin aure na. Safina kept calling me har sai da na daina daukan wayarta wai taji labarin daurin aure na and tana son mu shirya wani abu special ni da ita tunda muna da friends daya musamman yan secondary school din mu. Sai da taga na nuna mata bacin raina sosai sannan ta rabu da ni. Mustapha ma ya kira ni ban dauka ba, sai gashi ya turo min dogon message a Whatsapp wai yana yi min fatan alkhairi and he wants us to put everything behind us a cigaba da zumunci, and whenever I need a big brother he will be there for me. A karshe ya kara da cewa duk sanda nake bukatar a dan sassama min Mukhtar I should just give him a call. Ya rage kwana biyar daurin auren Safina ni kuma nawa shida sai ga Mommy ta kira ni. Na dauka na gaishe and she lost the words to say to me, sai kuma ta kama fada "yanzu wato da ban kira ki ba ke ba zaki taba daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kivi daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kiyi hakuri Mommy" ta cigaba "na dauka a ranar da muka taho yarinyar nan a ranar zaki fara nema na amma ke ko ajikin ki ma sai kika cigaba da sabgar gabanki ko?" Nayi shiru bance komai ba, ta cigaba "ance min nan da six days za'a yi miki aiki. Kina shan magungunan ki dai ko?" Na ce "eh ina sha" amma a zahirin gaskiya rabon da insha magani tunda ta bar kasar. Tace "good. Ki kula da kanki. Ki kuma kwantar da hankalin ki, kin san a haihuwa babu abinda ake gudu irin hawan jini" na yi shiru ban ce komai ba sai ta sake cewa "ko ba ki auri Mustapha ba still ke ya ta ce" nace "Nagode Mommy". *Him* Kwanakin sauri suke tayi a gurin Gidado, so yake su tsaya, dan ya samu at least ya shaki numfashi amma sun ki tsayawa and every day there is something to do. Gidan su already har ya fara cika da mutane musamman saboda bikin biyu za'a hada, gashi kuma bikin farko ne da za'a yi a gidan na su. Wannan ya saka a dole ya rufe dakin sa ya tattara ya koma gidan sa, gidan da aka fara siya masa yanzu kuma da ya takura aka sake masa wani. 8:00 PM Babu shiri Haidar shima ya tattara nasa kayan ya bishi, duk da hakan bai yiwa Gidado dadi ba dan yaso ya samu these days to himself dan in suka kare kuma shi kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da bai ma san ta inda zai bullo mata ba. Yana sane yaje ya kamawa abokansa da suka zo gari musamman dan bikin hotel rooms duk kuwa da cewa akwai wanna spare gidan amma shi so yake ya zauna shi kadai. Haidar din ma sai ya bude masa part din da ya kamata ace shine nashi, shi kuma ya shiga wanda ya shirya saboda Safiyya. Ya san cewa hakan da yayi ba karamin emotional damage zai jawo wa kansa ba amma ya zabi hakan. Babu komai na furnitures a gidan dan haka sai katifu suka je dasu suka shimfida suke kwana akai, sai kuma boxes din kayan sawan da zasu yi amfani da su da sauran abubuwan da zasu bukata. Kullum da safe yake fita gurin hidimomin sa and they kept his emotions on check har sai ya dawo gida tukunna, shi farko ya dauka in ya gaji bacci zaiyi saurin daukansa kamar yadda Ya Amen ya gaya masa, amma kuma sai ya ga shi ba hakan bane ba a gare shi. Ko ya gajin, in ya kwanta sai dai yayi ta juyi, amma bacci baya zuwa idanun sai gari ya kusa wayewa. Kullum a ransa babu abinda yake yin bita sai rayuwar sa da Safiyya, babu abinda yake so irin ya fahimci abinda yayi missing, ya fahimci inda hint din cewa tana da aure yake wanda yayi missing a baya amma ya kasa gani, Except kin kai shi gidan su da tayi. She kept on delaying and delaying giving all sorts of on delaying and delaying giving all sorts of excuses. Farko excuses din nata akan cewa tana gidan uncle dinta ne kuma uncle din zai yi mata fada in ya ganta da saurayi because yana tunanin cewa bata isa yin saurayin ba, daga baya da ya fara nuna mata shi fa da gaske aure yake son yi, aurenta yake son yi, sai ta koma yi masa maganar rashin lafiyar babanta and the fact that baya zama a kasar sosai, and ranar nan da ya takura mata she said bata son ta kaishi gurin uncle dinta sai dai babanta, saboda uncle din yana son hada ta aure da dan sa Mukhtar. Ya san Mukhtar. Tun the second haduwar su da Safiyya ya san Mukhtar, kuma tun a lokacin jikinsa ya bashi cewa something was going on at least a zuciyar shi Mukhtar din, tun sanda ya ganshi din kuma yaji cewa baya son sa. Amma kuma a zuciyarsa ya san cewa kishi ne yake yi. Ya san cewa kishi yana daga cikin weaknesses din sa akan Safiyya, yana da mugun kishin da har toro yake bawa kansa sometimes, ya kuma san kishin nasa a yanzu yana daga cikin abinda yake cin zuciyarsa. The memory of her dauke da cikin wani, knowing fully well abinda ya faru kafin a samu cikin shine babban abinda yake hana mishi bacci a yanzu. A yau ma bai dawo da wuri ba sai late, hopping to fall asleep as soon as possible, yana shigowa ma da yay packing bai shiga cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan. cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan jikinsa ya bar singlet ya zagaya bayan gidan yana jogging da niyyar karawa kansa gajiya. A bayan ne kuma yaga wani guri da Safiyya ta saka musamman ya ware mata bai yi paving ba "spices zan shuka a gurin, akwai spices din da ba a samu sosai a kasuwa ko kuma ba za'a samu fresh one ba, to gwara in samu seeds din su in shuka da kaina in ringa using". Ya tsaya a gaban clearing din yana hakin jogging din da yake yi. "damn you. Damn you Safiyya" ya fada a fili, sannan ya wuce da sauri ya cigaba da jogging din sa. Yana cikin haka yani alamar an bude gate, ya san Haidar ne ya dawo amma kuma baya son kowa yayi masa magana a yanzu, dan haka yayi sauri yayi kwana ya shige gidan ta kofar baya ya shige dakin da yake kwana. Direct toilet ya wuce ya kunna wa kansa shower ya rufe idonsa yana jin dadin sanyin ruwan. "'Komai zafi bana iya wanka da ruwan sanyi, mura yake saka ni" Yaji muryar ta kamar a yanzu take gaya masa, Ya tuna da amsar da ya bata a lokacin, "Kar ki damu, zan koya miki ne. Ita kan ta murar sai ta hakura ta bar mu". Ya fita daga shower din ya goge jikinsa, yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din, yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din, "Da wata farar fuskar ka anan" yayi murmushi. "Burge ki tayi" 4 8:00 PM Ya fito daga toilet din ya saka pajamas sannan ya karo karfin AC ya kashe fitila yayi addu'a ya kwanta, hoping to center his mind on something important, anything apart from Safiyya, amma babu abinda ya gani a idonsa sai Safiyya da ciki a office din sa. Babu kuma abinda yake son sani a lokacin sai abinda Safiyya take yi a wannan lokacin, babu abinda mind dinsa take saka masa sai different scenarios a abinda Safiyya take yi din. Ya mike tsaye ya kara wa kansa fanka sannan ya koma ya kwantatare da zagaye kansa da pillows, few minutes after that kuma ya sake mikewa zaune ya jawo wayarsa ya nemo number din Safina ya kira without realizing cewa karfe sha biyu ne na dare har da rabi. Sai da ta dauka sannan yayi realizing mistake din sa. "Hello Habibi. Ba ka yi bacci ba?" Ya matsar da watar daga fuskarsa yace "shit!" a hankali cikin jin haushin kansa. Sannan yace "hello? Uhmm, I think I made a mistake ba wannan number din zan kira ba" ta danyi shiru sannan tace "wa za ka kira to? By this time?" ya fara tunanin karyar da zaiyi, another of his weakness shine karya, bai iya karya ba kwata kwata. Yace "my friend, akwai wani friend dina Sahabi shi zan kira yanzu" ta sake cewa "by this time?" Yace "eh, baya bacci da wuri, nima haka" tace "ko dai ita zaka kira?" Ya dan bata rai "wa kenan?" Tace "your ex da ka fada min. Ko ita zaka kira Allah ya sa ka kira ni" ya danyi shiru sannan yace "I wish I can call her, there is nothing da ba zan iya bayarwa ba a yanzu to be able to call her. But she blocked my number. And beg me not to find another way to contact her. So to answer your question, ki kwantar da hankalin ki, ba ita zan kira ba". Tace "okay. Because I don't want to ruin the memory of the first time you call me da dare. Ba na son sunan wata ya shiga cikin memory din. It has always been a dream of mine. In ga ina waya da kai irin yadda yammata da samari suke y" yace "I told you abokina...." Tace "right. At least let me pretend ni ka kira. And since you called ya kamata mu danyi magana ai ko? At least tell me something about you da kake ganin ya kamata in sani, maybe about your friends or family ko aikin ka, anything, just talk to me " yace "okay. Let me start with the things I like, I like honesty, na tsani karya. I like tsafta a lot. Bana son hayaniya, bana son mita, bana son tsegumi ma'ana telling me something that do not concern me. And most importantly, I love my family, a lot" tace "yauwa, about the family, ban san su ba sam in banda Mufida, ita ma kuma a waya ne kadai ko hoton ta ban taba gani ba, ya kamata in san su ko?" Yace "zaki san su ai. A hankali, But the immediate family basu. al. A hankali. But the immediate family basu da yawa, daga Mama sai Abba sai Haidar and then Mufida. I am the eldest. Akwai cousins da yawa, I can't list them all. You will get to know them watarana" tace "haka ne. And your friends, aside Sahabi" yace "waye Sahabi?" Tace "Sahabi dai da zaka kira yanzu" yace "ohh that Sahabi, Sahabi my friend. Yes, akwai Sahabi and the rest. Zaki san su suma later. Now, let me call Sahabi kafin yayi bacci". Tayi ajjiyar zuciya "okay, shikenan. At least we are one step ahead. Good night Habibi". Sai dai daya ajiye wayar, maimakon ya koma ya sake gwada baccin sai ya tashi ya zauna ya dauko takarda da biro a cikin takardun da Abba ya bashi zai yi cike cike na sabon aikin da zai fara, ya juya bayan takardar kawai ya kama zane a jiki, zanen fuskar Safiyya. Sai da ya gama zana ta tas kamar zaka kira sunan ta ta amsa, sai kuma ya dukunkune takardar yayi jifa da ita ya koma ya kwanta. Da safe bai tashi da wuri ba dan baiyi bacci mai nauyi ba sai bayan sallar asuba, ya manta cewa a ranar zasu fita da Abba maganar chanjin aikin sa. He is going to take over some parts of managerial work na Company din Abba bayan bikin sa. Sai dai bai tashi ba har sai da Abban yazo gidan da kansa daukan sa kamar yadda suka shirya, ya kuma shigo har cikin gidan har dakin da yake kwance ya same shi yana bacci, takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya. takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya dauka ya warware. Sai ya samu guri a gefen katifar da Gidado yake kai ya zauna yana kallon zanen yarinyar da yake hannunsa. 8:00 PM Gidado yayi juyi sannan ya bude jajayen idonsa ya dora su akan Abba, sai kuma ya karasa bude don da sauri tare da mikewa zaune yana shafa fuskar sa a kokarin kore saurin baccin da yake kansa "Abba ka shigo? Ina kwana" Abba ya bishi da kallo sannan ya sake kallon takardar hannun sa. Sai lokacin Gidado ya lura da takardar, ya kara gyara zamansa yana shafa kai tare da kallon takardar da gefen ido. Abba ya nuna masa zanen tare da tambayar sa "Safiyya?" Gidado ya gyada kai bai ce komai ba. Abba ya nannade takardar ya ajiye a tsakanin su yace "ba ka son waccan yarinyar, zaka aure ta ne kawai saboda ni da mahaifiyar ka muna son kayi aure" babu alamar tambaya a cikin maganar dan haka Gidado bai bada amsa ba. Abba ya cigaba da cewa "abu na farko da na san ka riga ka sani shine we only want what's best for you. And right now, mantawa da wannan yarinyar shine the best thing for you" ya fada yana nuna zanen Safiyya with bitterness in his voice, abinda yake nun irin haushin Safiyya da yake ji a ransa. Ya cigaba da magana, "mun yanke shawarar aure shine babban abinda zai taimaka maka wajen mantawa da ita maka kayi moving forward. Sai dai daga ni har mahaifivar ka are not perfect, kuma. ni har mahaifiyar ka are not perfect, kuma bama ganin gaibu, zata iya yiwuwa abinda muka zaba maka ba shine alkhairi a gare ka ba, amma ni na san wanda yake perfect wanda kuma ya san gaibu, Allah. Ina son zan baka wani assignment, idan kayi shi dai dai zaka samu reward mai girma. Ina so kuma inyi maka wani alkawari. A cikin kwanakin nan da suka rage kafin daurin auren ka, ina so kayi istikhara, idan har kafin daurin auren ka cigaba da jin a ranka cewa still ba ka son aure to ka gaya min, ko da kwana daya ya rage zan dakatar da abin domin ya tabbata ba alkhairi bane ba. Amma idan kaji a ranka cewa ka amince kana son auren yarinyar, to sai mu cigaba da shirye shiryen mu har mu tabbatar da faruwar abin". Ya mike tsaye yana kallon sa yace "ka tashi ka shirya, your new job awaits you ", Gidado ya karbi shawarar Abba sosai, dan tun da suka yi maganar ya dukufa da yin adduoin neman zabin Allah. Babu dare babu rana. Ya kuma cigaba da shirye shiryen duk da suka kamata na bikin. Yan'uwansa sunzo na kusa da na nesa, maza da kuma mata. Da yake Abba da Mama first cousins ne sai ya zamana yan uwan duk daya ne babu banbanci, duk kuma treatment daya ake basu. Yan'uwansa samari da suka zo gari suka kuma fahimci a gidan da yaje ya boye kansa duk sai suka tattaro suka dawo gidan, sa'annin Gidado suna bangaren da yake while sa'annin Haidar suma suka tare a bangaren da yake. Gidado bai ji dadin haka ba saboda an takura masa an hana shi zama yayi hira shida zuciyarsa, shi da safiyyan shi. Sai dai kuma a wani bangaren yaji dadin hakan dan cikin kwanaki biyu kacal sai gashi yana hira da dariya sosai a cikin su. Wani lokacin idan suka nutse a cikin hira har mantawa yake yi da cewa wai aurensa ake yi, kuma wai baya son yarinyar da zai aura. Sai dai kuma yana iyakacin kokarin sa gurin danne wa dan baya son yanuwansa su fahimta har suyi ta yayata maganar a cikin dangi. Sai dai kuma yanuwan are making it extra difficult for him. Casually someone would ask him "ina yarinyar nan kuma da ka susuce akan ta kwanan baya?" His answer to that question was always "Allah yayi mata rasuwa" daga haka ba sa sake tambayar sa. In wani ma ya dauko tambayar sai a samu In wani ma ya dauko tambayar sai a samu wani ya hana shi dan kar su taba wa angon feelings din sa. Sometimes kuma su kan tambaya "wannan gidan na ka ai yafi wancan girma Gidado, me ya sa ka chanja?" And shi kuma ya kan amsa musu da cewa "amaryar ce tafi son wancan". Alhalin ita amarya ko gain gidan ba ta taba vi ba sai da masu yi mata jere suka je suka yi suka dauko mata pictures da videos. Gidan da za'a kai amaryar mai kyau ne, dan sosai iyayensa suka nuna masa gata a siyan gidan kamar yadda suke nuna masa gata a komai. Part dinsa daban na matar daban sannan a waje kuma akwai bangaren baki maza sannan da part din ma'aikatan gida (boy's quaters). A bangaren sa akwai bedrooms biyu da parlor, a nata bangaren akwai bedrooms uku da parlor. Part din bakin kuma parlor ne karami da dakuna biyu. Kamar yadda iyayen ango suka yi kokari wajen kure adakar su akan gidan Gidado haka bangaren amarya su ma suka yi nasu kokarin, dan duk dakunan da suke part dinta babu inda ba'a cika shi da kaya ba, kaya kuma na gani na fada wa da suka yi dai dai kuma suka dace da tsaruwar gidan. Abin har sai da ya bawa dangin angon mamaki, dan a binciken da suka yi wa iyayen amarya basu samu labarin cewa suna da irin wannan kudin ba, A bangaren amarya tun a week to bikin A bangaren amarya tun a week to bikin Mommy ta tafi can Katsina suka cigaba da kammala shire shiryen su, duk wani shiri da za"a yi wa amarya na gyaran jiki anyi wa Safina shi, ita kanta ta san tana da kyau, ta kuma shirya siye zuciyar angon na ta da wannan kyan nata da kuma duk kan wata kissa da kisisina da Allah ya halicci mata da ita. Ta san cewa akwai challenge a gabanta amma kuma ta shirya karbar sa hannu bibbiyu dai har zata samu muradin zuciyarta. Ta yarda da kalmar hausawa da suke cewa mahakurci mawadaci. Mommy tayi mata shirin duk da akeyi na gyaran amare dan taimaka musu wajen sauke hakkin aure da zai hau kansu, amma Mommyn ba ta san cewa ita ma da kanta Safinar ta gama siyan duk wadannan kayan har ma da wadanda suka fi na Mommyn. A shirye take tsaf da yin amfani da dukkan baiwar da Allah yayi mata wajen ganin ta mallaki Habibin na ta. 5 + 1 4:15 PM anar Lahadi ta tafi garin Abuja. A ranar ne kuma bayan kiran wayar angon sau ba adadi kamar yadda ta saba kullum ba tare da kiran ya shiga ba sai ta tura masa message. "Na shigo Abuja, Dan Allah ka zo in ganka, Ina gidan Hajiya" Sakon ya shigo masa ya karanta ya rufe ya ajiye, A ranar da ya rage saura five days daurin aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara. aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara cika fiye da kullum, yan uwan sa da suka 20 gari suma sun gayyato abokan su da suke gari, wasu abokan kuma sun gayyato nasu abokan. Gidan ya zama kamar wani dan karamin biki ake yi amma na maza zalla. Mama kuma ta daure musu gindi ta hanyar aiko musu da kulolin abinci kala kala. Daga nan sai hira ta balle, aka fara zancen aure da rayuwar cikinsa da challenges din sa, masu auren ciki suna baje fasahar experience din su, yayin da samari suka baje kunnuwa suna daukan darasi. Wannan ya sa angon ya zame ba tare da sun sani ba ya fice ya bar musu gidan. Sai da ya shiga motar sa kuma sannan ya fahimci bashi da gurin zuwa, dan duk friends din sa da zai iya zuwa gurin su suna cikin gidan sa, a lokacin ne sakon Safina ya sake shigowa. "Na gama abinda zanyi a Abuja. Gobe aka ce in koma. Dan Allah ka shigo". Ya rufe idonsa yana tunani for some seconds sai kuma ya bude ya kira number din ta. Tana dauka yace "gani nan zuwa" bai jira amsa ba ya katse kiran. Mintuna kadan suka kaishi kofar gidan, mai gadi ya taho da sauri da fara'a a fuskar sa amma sai Gidado ya bata rai tare da daga masa hannu alamar baya bukatar zuwan sa, sai da mai gadin ya juya sannan kuma sai yaji babu dadi a ransa tunda mutumin bai yi masa komai ba. Ya dauko wayarsa ya sake kiranta "ina waje" yace tare da sake ajiye wayar. Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye da hijab fuskarta babu kwalliya. Ta bude kofar gaban motar ta shiga ta zauna, sai ya dauke kansa yana jin haushin ta zauna a seat din Safiyya. Amma kuma ai shi ya kira ta. And only God knows me Safiyya take yi with her husband, why won't him enjoy himself too? Ta fara mishi magana "har na fitar da rai na dauka ba zaka zo ba. But now I am glad tunda kazo" ya juyo yana kallon ta fuskarsa a matukar daure yace "me yasa kike nemana?" Tana kallon sa tace "what's with that face? Ko nayi wani laifin ne kuma ban sani ba, I just wanted to see you kuma banga abin laifi dan ina son ganin ka ba". Yace "what's wrong with my face? I thought ita kika gani kika ce kina so" ta sunkuyar da kanta kasa fuskarta tana nuna damuwa tace "na san nina ce ina son ka ba sai ka goranta min ba. Kawai naga ranka a bace ne. Ni face din da nayi falling in love with is always happy always smiling" yace "you better get use to the unsmiling face. Because you are going to see a lot of it" suka yi shiru gabaki daya, sai da aka jima sannan da dago kai tace masa "dama nazo gari ne zanyi kunshi da saloon, and da akayi min kunshin sai na ga yayi kyau sosai, and I thought ya kamata kai zaka fara gani, I never thought hakan zai zama laifi". Yace "are you telling me kin taho tun daga Katsina zuwa Abuja kawai dan kiyi kunshi? Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu. Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu yi miki ba?" Ta dago kai tana kallon sa tace "actually, na fadi haka ne kawai a gida dan su barni in taho, Mommy like classy things and ta san a Abuja zan fi samun taste din ta, but in reality I just wanted to get away from her" yayi mamakin jin haka yace "why?" Tace "fada. Tun da taje Katsina take yi min fada. She is not happy with this marriage saboda bata san ka ba, she kept complaining cewa bata san sanda muka hadu ba ballantana sanda muka saba har zamu yi aure. Farko bata kasar, da tazo cewa tayi sai an daga. Da kyar ta yarda za'a yi din" tayi shiru tana jujuya hannunta sannan tace "she said you don't love me. Tace ko waya bata ga muna yi ba. There is no love vibes at all". Ya juya fusakarsa yana kallon window, sai kuma ya juyo yace "you know our agreement. And you agree with my conditions" tace "yes, I know. And ba complain nake maka ba. I just need a little bit of gesture from you. At least make it easy for me". Yace "let me ask you a question. 5 4:15 PM Why do you agree to this? Me yasa kika saka kanki a wannan situation din?" Tayi shiru tana tunani sannan tace "I love you, That is all that I know, Kuma na san I am an easy going person, bani da matsala, You may not love me know saboda yarinyar da kake so, but eventually you will fall in love. kake so, but eventually you will fall in love again. And the easiest way to make you fall in love with me is to marry you. Yanzu misali ita yarinyar da kake so din, I don't want to know her name, idan da zaka samu chance din auren ta even though bata son ka, won't you take the chance?" Yayi shiru yana tunani, sai kuma yayi sauri ya kawar da tunanin daga ransa yace "she loves me, so I can't relate to that" tace "she loves you and she left you?" Bai amsa ba sai ya dauke kansa gefe yana kara jin haushin ta, amma kuma yasan abinda ta fada gaskiya ne, shi kansa kuma a yanzu bashi da tabbas din in Safiyya tana son sa. Suka sake yin shiru a motar sannan yace "if that's all. Zan koma. I have things to do" tayi ajiyar zuciya "Okay. Nagode da ka samu damar zuwa. Ina neman alfarma amma guda daya. Please ka bari in ringa kiran ka. At least saboda hankalin Mommy ya kwanta" ya bata pan't you call someone and pretend cewa da ni kike? I am a little bit busy for phone calls" ta dago ido tana kallon sa, kawai sai yaga hawaye yana bin fuskarta, ta saka hannunta da ya sha kunshin amare yayi kyau a farar fatar ta ta goge hawayen sannan tace "okay, Na fahimta, Thank you", Ta bude kofa zata fita sai kuma yaji babu dadi a ransa yace "Safina wait" ta dakata amma bata juyo ba sai dai yana jin alamar kuka take yi yace "I am sorry, Okay, Zamu ke. kuka take yi yace "I am sorry. Okay. Zamu ke yin waya. Sai menene kuma kike so" ta juyo hawaye yana cigaba da zuba a fuskar ta tace "at least stop being mean to me. Ko baka nuna min soyayya ba ka daina wulakanta ni. It hurts a lot. You have no idea how much I have sacrificed for this relationship. The least you can do is to be nice to me". Bai sake magana ba ta fita daga motar ta rufe masa kofa. Sai da yaga ta shiga gida sannan ya tayar da motar ya tafi yana jin zuciyarsa duk tayi masa nauyi. Baya jin da din yadda yake treating yarinyar amma baya iya hana zuciyarsa gaya mata abinda yake cikin ta. Kuma kamar yadda ta fada masa, ko da bai so ta ba the least he can do is to treat her nice. Treat her kamar yadda yake treating sauran mutane, or more. Albarkacin tarin soyayyar da take yi masa. Gidan Abba ya wuce, ya tarar ana kokarin shiga sallar magrib sai ya bisu suka yi sallar itare ayan sun fito daga masallacin ya samu ya shiga ciki ya gaishe da sisters din Mama da ya gani a parlor sannan ya wuce cikin bedroom dinta ya gaishe ta itama. Har ya tashi zai tafi sai ta tambaye shi ko akwai abinda yake bukata yace a'a, sai kuma ta sake tambayar sa "ya kuke ciki da Safina kuwa? Kuna waya ma kuwa?" Ya dawo ya durkusa yana shafa kansa yace "yanzu ma daga gurinta nake. Tazo gari taje gurin kunshi" Mama tayi murmushi, yaga alamar jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to madalla, hakan yayi kyau sosai. Allah yayi maka albarka" yace "Amen" a ransa yana jin dadin abinda tace din sosai. Tun a mota kafin ya bar gidan ya cire wayar sa daga do not disturb din da ya saka ta saboda Safina. Washegari da safe da ta kira shi sai kiran ya shiga ta sanar masa cewa zata koma shi kuma yayi mata fatan alkhairi. Da ta sauka a Katsina ma ta sake kiransa ta gaya masa cewa ta isa, yayi mata sannu, sannan reluctantly yace ta gaishe masa da Mommy. Daga nan suka fara magana, sama sama, yana replying messages dinta in ta kira kuma yana amsawa. A haka har ta turo masa hoton kunshin da aka neme shi musamman dan a nuna masa amma yaki gani, and he replied with "yayi kyau". Kamar yadda aka tsara ranar alhamis aka fara biki akayi kamun amarya a can katsina a gidan wan babanta. Mommy ta gaiyaci mutanen ta sosai sun je anyi komai da su, yan uwan ango ma an ware representatives sunje anyi kamun a gaban su a inda kuma suka samu tarba ta musamman daga gurin Mommy dan sai da ta tabbatar ta fitar da yar tata daga kunya a idon su. A 4:15 PM A ranar kuma aka shirya za'a yi kamun ango shima a nan Abuja, Sai dai kuma, tun. tun a safiyar ranar ne da samari yanuwan ango suka tashi a gidan da suke zaune tare da shi sai suka neme shi suka rasa, sai maigadin gidan ne ya gaya musu cewa tun assubar fari ya fice daga gidan a motarsa. Aka yi ta kiran wayar sa kuma bata shiga. Wasa wasa har rana ta yi sosai babu ango babu labarinsa. Tun suna boyewa suna cigaba da bincike su kadai har suka sanarwa da iyaye halin da ake ciki. Ango ya gudu. Ana ta kiran wayarsa kuma tana ta ringing amma baya dauka. Farko duk wanda aka gaya wa cewa ango ya gudu sai yayi dariya thinking cewa wasa akeyi, sai daga baya kuma sai a fahimci cewa babu wasa a cikin lamarin. Neman duniyar nan akayi wa angon aka rasa shi har lokacin kamun yayi. A gidan kakannin su aka tsara cewa za'a yi kamun. Amma rashin gain angon ya saka aka tattaro aka dawo nan gidan su angon ana ta lissafin yadda za'a yi, auntyn sa Maimoon sai dariya take yi dan ita dai ta san Muham had Gidado ba zai bata ba kamar wani key din mota, yayin da Aunty Amina ta dage sai fada take yi akan ya basu kunya sun tara mutane ya gudu ya bar su, da ya san ba zai tsaya kamun ba ai da sai ya fada musu da wuri su san abin yi. Hafsat kuwa sai kallon su kawai take yi dan dama ita bata ga amfanin kamun nan ba, daga baya dai da taga magana taki ci taki cinyewa sai ta kira Al'ameen ta zare masa ido tace sai ya fadi inda Gidado ya shiga, yayi ta rantse rantsen cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta. cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta fahimci da gaske yake sannan ta rabu da shi. Ana cikin haka Abba ya shigo, ya zauna yana binsu da kallo yana murmushi. Amina ta kalle shi tace tabbas yasan inda Gidado yake tunda bai nuna ya damu ba. Yace "to ni akan me zan damu? Tsakanin ku ne da shi ni babu ruwa na. In kuka kama shi duk abinda kuka ga dama kuyi masa" sai kuma ya saka hannu a aljihu ya dauko wayarsa ya kira number din Gidado, shi ya san indai da ran Gidado da kuma lafiyar sa babu yadda za'a yi ya kira shi yaki dauka. Yana kiran nasa kuwa ya dauka din, direct yace masa "kana ina?" Gidado yayi shiru kamar ba zai amsa ba sannan yace "ina daki na" yace "wanne dakin?" Yace "dakina na gidan mu". Abba yayi shiru yana jin yadda muryar Gidado tayi kasa sosai, and he can almost feel halin da zuciyar dan nasa take ciki. Yace "iyayenka suna neman ka zasu kama ka" Gidado yace "Abba ni da ba criminal ba me nayi da za'a kama ni?" Abba yace "tsakanin ku ne wannan. Ni dai yanzu ka ban amsa ta. Za'a yi ko ba za'a yi ba mu?" Daga Gidado har abban nasa sun fahimci cewa ba wai maganar kamu suke yi ba yanzu, Gidado ya sake yin shiru. Abba yace "yau kadai ta rage maka" still bai ce komai ba, Abba yace "ina jin ka" Gidado yace a hankali "za'a yi. Na amince ayi". hankali "za'a yi. Na amince ayi", Daga nan Abba ya katse wayar ya juya yana kallon yan'uwan nasa da suka saka shi a gaba suka tsare shi da ido. Ya kalli Amina yace "na ga kin damu dai da cewa sai kin jika yaron nan da nono, me zaki bani idan na gaya miki inda yake?" Tayi shiru tana tunani sai kuma tace "in dai ka gaya min inda yake daga yau zan dinga gaishe da matarka ina ce mata yaya" duk suka kwashe da dariya. Shekara da shekaru dama suna wannan rigimar tsakanin Amina da Zainab. Zainab kamar kanwa take a gurin Amina amma kuma mijinta kamar Yayan Amina ne (if you know you know ») dan haka kowa a cikin su ya dage lallai sai dayan ya bashi girma. Abba ya mike tsaye yace "yana dakin sa" sannan ya fice ya bar musu gidan. Ai kuwa Amina ta sunkuci turaren da ta taho dashi tayi dakin Gidadon sauran yan'uwa suna binta, taje kuwa tayi ta gudun kofar duniyar nan yaki budewa sai da Mammy tayi masa magana tare da yi masa alkawarin ba za'a zuba masa nono akai ba sannan yayi Ami la A bangaren Gidado ranar tun da assuba daya tashi ya yanke shawarar amsar da zai bawa Abba, Saboda shine abinda yaji hankalin sa yafi kwanciya dashi, bawai dan yaji a ransa yana son Safina ba, but yaji a ransa cewa auren shine abinda ya dace dashi, shine abinda hankalin sa ya kwanta dashi a wannan lokacin, The decision made him sad but free at the same time. Sad that he will have to made the final acceptance of the fact that Safiyya ta bar shi har abada, that his life has changed forever. Wannan yasa ya lallabo ya shigo gidan su ya shige dakin sa ba tare da kowa ya ganshi ba, making sure cewa ya boye motarsa a inda ita ma ba za'a ganta ba. Farko kwanciya yayi yayi baccin sa sai azahar ya tashi yayi sallah sannan ya kama yin aikin da yazo dakin da niyyar yi, aikin tattare duk wasu kaya nasa da duk wani abu nasa da yake da dangantaka da Safiyya, including his phone and his laptop da suke cike da hotuna da pictures dinta, ya hada su ya zuba a wata locker ya rufe. A binciken nasa ne ya dauko wata rose flower single stem da Safiyya ta taba bashi. Ya tuno lokacin da ta bashi din da kuma dalilin da ya sa yake ta ajjiye da ita. Suna tafiya ne ranar nan a hanya kamar kullum yana yi mata korafin har yanzu bata kai shi gidan su ba, kar yaje ayi mata miji a gidlan su a raba shi da ita tunda ba'a san shi she kept telling him cewa ba za'a iya raba su ba amma a karshe yace dai shi bama shi da tabbas din tana son sa da gaske ba wasa take yi masa da hankalin sa ba, suna maganar ne tayi ta tsinkar flowers a jikin bishiyoyi tana hadawa, sai da ta tara da yawa sannan ta cire ribbon din data daure gashinta da shi ta daure flowers din da shi ta bashi, tace symbol ne na son da Safiyya take wa Muhammad, Yaji dadi sosai kuma ya. take wa Muhammad. Yaji dadi sosai kuma ya karba, but He jokingly said "wannan ai gaibu ne, ana jima wa zasu yi wilting su bushe su mutu. I need something that is a forever thing. Wanda zai nuna min matsayina is a forever one a gurin ki. Something like zuwa gaishe da Daddy", A week after that, a jewelry company delivered that rose to him. Single stem ne na kyakkyawar red rose flower. An nannadeta da transparent plastic sheet. A jikin sheet din anyi rubutu da golden color in her own handwriting. Muhammad, This feeling is a forever thing. Your's Piya Amma abinda ya saka shi mamaki a lokacin shine kasancewar jewelry company ne suka yi delivering sakon. Sai da ga baya ya fahimalalili. A kasan rose din, dan box din da aka zura stem din rose din a ciki, was made of gold, pure gold molded into the shape of a heart with their initials scribbled on it "MS". It was too much of a gift da yaji a ransa cewa bai kamata yayi accepting ba, that gold is a fortune, Ya tabbatar a gida ba'a san tayi wannan kyautar ba, Amma kuma he. san tayi wanna kyautar ba. Amma kuma he so much love it da ya kasa mayar mata. Wannan ya sa ya boye ta a inda yasan babu wanda zai ganta da niyyar in sunyi aure sai ya bata abinta. But now it is never going to happen. Sai ya samu kansa da jujjuya rose din a hannun sa yana wondering me zaiyi da iya yanzu. A karshe sai ya koma kan gado ya kwanta rigingine ya dora rose din akan kirjinsa ya rufe idonsa. Yana jin wayarsa tana ta kara, kuma a ransa ya san cewa nemansa ake yi amma haka yayi ta kwanciyar sa, sai dai damuwar sa bata saka a ransa yaji cewa ya fasa yin auren ba. A haka akayi la'asar ya tashi yayi sallah ya koma ya kwanta, deciding cewa ba zai je gurin kamun sa ba. Duk wadanda suke kiransa yana gani, kuma ya yanke shawarar ba zai dauka ba. A haka har wanda ba zai iya kin daukan wayar ta sa ba ya kira shi. Ya dauka, ta tambaye shi game da decision dinsa kuma ya gaya masa amsar. Bai jima da ajiye wayar ba yaji bugun kofa da kuma muryar Aunty Amina tana mishi magana filatanci "na san kana ciki, ka bude kofar nan" ya tashi zaune yana dafe kansa, Suka cigaba da hayaniya da kuma bugun kofar. Bai ce musu komai ba sai ya tashi ya kammala adana dukkan kayan da yake bukatar adana wa including the forever rose sannan ya tsaya a bakin kofar, a lokacin yaji muryar Mammy tana masa magana, Yayi murmushi ya amsa mata da fulatanci. murmushi ya amsa mata da fulatanci. "'Amma banda nono za'a zuba min" tace "eh banda nono" yace "kinyi alkawari?" Tayi dariya tace "nayi alkawari" sannan ya bude kofar, yana budewa suka feshe shi da turaruka kala kala sannan aka dauki guda. Duk da cewa turarukan sunyi masa karfi aka, amma sai ya samu kansa da yin murmushi yana jin dadin gain iyayen nasa cikin farin ciki. 6 4:15 PM Zuwa dare sai gashi yana hira a cikin su harda dariya, ranar gabaki daya familyn anan suka ci abincin dare sannan suka raba dare suna hira, sai da bacci ya fara cin karfin sa sannan ya zame jikinsa ya koma dakinsa ya kwanta acan. Da safe ya tashi da wuri kamar yadda aka tsara ya shiga wanda, saboda da wuri zasu tafi gurin daurin auren, yana fitowa daga wanka da bathrobe a jikin sa sai ya ga Mama a zaune akan gadon sa da kayan sawa na maza a hannunta tana fesa turare a jiki. Ya rissina ya gaishe ta yana jinsa wani iri saboda bu kaya a jikinsa amma sai yaga ita ko an xinta, Ta mika masa kayan hannun ta, fuskarta dauke da alamar damuwa, tace ."ga kayan da zaka saka nan. Dan banga ka tanadi kayan sakawar yau ba" ya karba tare da yi mata godiya, bata amsa ba sai tace "kayi sauri ka shirya, baban ku har ya shirya" ya ce "to" amma sai ua cigaba da tsaiwa da kayan a hannun sa tunda dai ai ba zai saka kava a cabanta ba, zai saka kaya a gabanta ba. Ta mike a hankali kamar bata son fita. Har takai bakin kofa sai kuma ta juyo tana kallon sa tace "Muhammad?" Ya amsa, sai tace "are you happy?" Yayi shiru yana kallon damuwar da take rubuce a fuskar ta sai ya girgiza kansa yace "no, I am not happy Mama. But I am contented, alhamdulillah" tace "good. That's a good start. Allah yayi maka albarka". Sai da ta fita sannan a hankali yace "Ameen Mama" Ya shirya ya saka kayan da Mama ta bashi. Farin yadi ne tas da akayi wa aiki mai kyau kalar ruwan toka mai haske, wanda ya dace da hula da takalmin da ta ajiye masa. Ya tsaya a gaban madubi yana kallon yadda yayi kyau, shi kansa ya san yayi kyau ba kadan ba. Ya tuna maganar Safiyya "You will look so good in white" Sai yayi murmushi. "Good bye Piya". Daga nan ya juya ya fita tare da rufe kofar dakin, kna wing he will come back a changed man, al tried man. Maybe even a happy man. Abinda bai sani ba shine a yanzun ne zai bude babi mai cike da rikici da sarkakiya a rayuwar sa, Yanzun ne matsalolin zasu fara, *Her Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina. Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina lissafa su a matsayin kwanakin da suka rage a daura min aure da Mukhtar, amma kuma lakaki suke yi idan na kalle su a matsayin ranakun da suka rage ayi min aiki a raba ni da abinda yake ciki na. Duk shire shiryen aikin sun kammala a asibitin da za'a yi, sun dauki dukkan vitals dina sun tanadi dukkan abinda suke ganin zan bukata. Sun kuma tanadi dukkan abinda babyn da za'"a ciro zai bukata tunda zai zamanto premature ne kuma zai bukaci kulawa ta musamman. Yayinda ni kuma na kammala dukkan shiryen shiryen bayar da babyn kamar yadda na riga nayi niyya. Sharuda na sune bana son ganin shi, bana son Daddy ya ganshi, bana son kuma in an samu parents din da suke son sa a basu wani information da ya shafe ni ballantana har nan gaba yayi amfani da information din gurin sanin ko ni wacece. A gida kuma kullum muna cikin rigima da Daddy, muyi rigima yayi fushi ya sauko da • kansa ko kuma ni inyi fushi ana jima wa kum sauko inje in bashi hakuri. Duk da ya amine da maganar Mukhtar amma yaki hakura da kokarin chanja min ra'ayi na. Sannu kuma har yanzu bai yarda da magana ta ta cewa ba zan koma Nigeria ba. He kept saying akwai plans din da ya shirya min in na koma Nigeria, But he wouldn't say what. Mutanen kadai da nake samun fahimtar juna da su sune twins, Kullum sai muni hirar mu a waya. Suna kuma updating dina akan duk. a waya. Suna kuma updating dina akan duk abinda yake faruwa a gidan. Su suka bani labarin rikicin da ake tayi tsakanin Mommy da Safina, a fahimtar su ita Mommy hankalin ta bai kwanta da wanda Safina zata aura ba. A kalaman ta kamar yadda suka fada min "shegen girman kai ne da shi da isa kamar wani dan sarkin Makkah" Sun so Daddy ya bar su su taho su zauna tare da mu amma yaki, ni na fahimci baya son Mommy ta sake jin haushi tace ya kwace mata su, shi lallai so yake a daidaita. Kusan kullum kuma in muna waya sai sunyi min maganar Hajiya, tana ta damn su da tambaya akai na, ta damu da ni, musamman da taji cewa za'a daura min aure. "Kin san bata san halin da kike ciki ba. Mommy bata gaya mata ba. Tace Hajiya bakinta bashi da linzami" 6 2 4:15 PM 1 '"Bata gaya mata ma maganar rikicin da suka yi da Daddy b dasan idan da ta gaya mata 'da zata iya yi yaya Safina kayan daki amma kuma da kowa a gidan bikin sai yaji labari" Nayi murmushi, a yarda da maganar Mommy a nan, Hajiya tana da kirki sosai, ammà indai magana ta shiga ta kunnen ta to sai ta fita ta bakin ta, Kuma ba wai da niyyar munafunci ba. Haka Allah yayi ta bata san wani abu wai shi sirri ba, Da ake zata san da. wani abu wai shi sirri ba. Da ake zata san da zancen cikin nan nawa, zata tausaya min sosai ta bani dukkanin kulawa, bayan ta gamai min fada, amma kuma kowa da yake gidan da wanda zai shigo gidan sai ya san maganar. Safina har da turo min pictures din gidanta sanda aka gama jerenta, sannan tayo min message din godiya. Ranar kamun ta ma haka ta turo min pictures din kyalliyar da tayi, telling me that taso ace ina nan. Sannan sai washegari, washegari ranar daurin aure. Ranar dama ban samu baccin kirki ba saboda lissafin rayuwa. Haka na gama daren akan sallaya ta. Gari yana wayewa nace saura kwana daya. Ina nan kan sallayar har lokacin in abincin Daddy yayi naje na hada masa, yanzu baya iya cin abinci mai tauri sai mai ruwa ko kuma wanda aka dafa yayi laushi sosai. Naje na kai masa na tashe shi zaune ya dauka yana ci, baya son inke bashi abinci a baki yace cin abincin da kansa ma wani exercise ne. Yana ci yake tambayata ko na gaml da kaya na na zuwa asibiti nace masa na gama, dama da yamma zan tafi, a can zan kwana. Ya sake tambayar ko akwai abinda nake bukata nace masa a'a. Ni kuma na sake yi masa maganar cewa bana son ya bini asibiti gwara yayi zamansa a gida tunda Aunty Hajjo zata je amma ya nuna min ba zai zauna a gida ba, Sometimes na kan yi tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk. tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk kuwa da cewa shi kullum cewa yake yi a gurin Ammi ne. Sai da nurse din shi yazo ya hada masa ruwan wanka zai taimaka masa yayi sannan na fita na koma parlor na zauna. Gaba na sai faduwa yake yi. Nayi tunanin maganar aiki na ce take damuna amma kuma ban taba damuwa da ita ba why will I now. Ina nan zaune har wajen azahar nurse din ya fito yace zai je ya dawo, ni kuma na tashi na shiga kitchen zan nema mana abinda zamu ci da rana. A lokacin ne wani tunani ya fado min. Twins sunce 11am za"a daura auren Safina. Na kalli agogo naga 12:30 ma'ana 11:30 kenan a Nigeria. Sai nayi tunanin ko an daura? Na shiga kitchen din na dora abincin sai na dawo daki nayi sallah kafin abincin ya kammala., Sai da na idar nayi adduoi na sannan na dauko waya ta zan duba ko twins sun turo min labari. Ina shiga kuwa naga méssage from Hussein. "'Yaya an daura auren Yaya Safina. We are missing you here ke da Daddy" Naji babu dadi a raina, nima ina missing din su, Sai naga ya dora status, nayi sauri na bude dan nasan pictures din daurin auren ne, A lokacin ne na ganshi, A lokacin ne na ganshi. Sai da na ajjiye wayar na saka hannayena biyu na murza idona dan in kawar da gizon da yake min, saboda kwanan nan ba a mafarki ba har a ido biyu gizo yake min in ganshi kamar ya shigo gidan ko kuma inji kamar muryarsa. Na sake daukan wayar na sake dubawa. Muhammad ne, Muhammad dina, yayi kyau fiye da yadda na taba tunanin zai yi. Yana tsaye Hussein yana tsaye shima a kusa da shi. Hussein yayi captioning hoton with "Nayi sabon wa" Menene wa? Shine tambayar da na fara yiwa kai na. Me Muhammad yake yi a gurin daurin auren Safina? Sai dai hoto na gaba shi yayi kokarin amsa min tambaya ta. Muhammad din ne dai again, this time sho da H an da Hussein. Hussein ya rubuta "With the groom. Allah ya sanya alkhairi" Naji cikina ya daure, kwakwalwa ta ta toshe. Na sake tambayar kaina "menene groom? Me kalmar groom take nufi?" Hoto na gaba ne ya hau da kansa ba tare da na tura shi ba, Muhammad ne a tsaye da Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliva cikin farin. Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliya cikin farin lace din da na siya mata. Fuskarta dauke da tsantsar farin ciki. A kasan hoton Hussein ya rubuta. "Amarya da ango" 89 7 3 3 4:15 PM Na ajiye wayar tare da girgiza kaina kamar mai kokarin tashin kaina daga bacci, amma kuma ba baccin nake yi ba. Na dafa gadon da yake gaba na na mike ina jin kamar kaina yafi dukkan sauran jiki na girma saboda kamar dukkan jinin jikina ya tattare ya koma cikin kan, shi kansa bugun zuciya ta a cikin kai na nake jin sa. In dai har da gaske ba mafarki nake yi ba, ba kuma haukacewa nayi nake hallucinations ba, to tabbas auren Safina da Muhammad Gidado aka daura shi. Na dafa bango na fara kokarin fita waje sai, kuma na dawo dakin na dauki handbag dina da take ajjiye akan side drawer na rataya, na cigaba da laluben hanya har na fita parlor. "Daday!" Na fada da karfin da bansan ina da shi ba. Na cigaba da tafiya ina gain gaba na yana kara duhu duk kuwa da ba dare ne yayi ba, Sama sama naji muryar Daddy yana magana, "Safiyya! Lafiyar ki, Me ya faru? Ina zaki je" na juyo inda naji sautin muryarsa nace "gida zanje, Nigeria zan tafi, Daddy Muhammad ne fa, Wallahi Daddy shine. Muhammad ne fa. Wallahi Daddy shine. Daddy mutuwa zanyi. Daddy zuciya ta zata fashe. Daddy mutuwa zany" na cigaba da fadar sauran maganganun da ban san me nake cewa ba yayin da jiri ya debe ni nayi kasa. Dishi dashi naga motsin Daddy ya mike daga kan wheelchair dinsa yayo kaina, sai dai kafin ya karaso ya yanke jiki ya riga ni kaiwa kasa. Sai da kaina ya daki center table din gurin sannan ya karasa kasa. Na hango Daddy ya sake yunkurawa zuwa inda nake fuskarsa da cike da tashin hankali. "Not my daughter. God please take me instead" ya fada a hankali. Sannan kuma da karfi yace "who is there? help us please. Help!" A hankali na sake ce masa "Daddy Muhammad ne". Sannan na rufe ido na into nothingness.... Longest episode ever Shin kina son wannan episode din ya zamar miki taliyar karshe ko kina son kari....... .... Muhammad dai ya auri Safina, while madly in love with Safiyya, ba tare da yasan. Shin kina son wannan episode din ya zamar miki taliyar karshe ko kina son kari.......... Muhammad dai ya auri Safina, while madly in love with Safiyya, ba tare da yasan dangantakar dake tsakanin Safina da Safiyya ba. Ga Safiyya kuma ta dauki hanyar lahira bamu sani ba ko zata yi rai ko akasin haka. In bata tafi lahirar ba ma she is set to marry Mukhtar Yaya wanna badakalar zata kare Yaya wadannan aurarraki zasu kasance. Menene ainahin labarin Safiyya da mahaifiyar ta Menene dangantakar su da Mommy And above all, wanene uban cikin jikin Safiyya. Kina son wadannan amsoshin? Na tabbatar kina so, Turo naira 500 dinki zuwa wannan account din 0779484.494 Nafisa Tafida Usman Access Bank - Safiyya' owner 8:51 PM Episode Sixteen: Junior Kukan jariri ne sound din da ya fara ratsa consciousness dina, kamar a cikin kai na aka saka min jaririn, kamar a cikin kwakwalwa ta yake kukan cikin kokarin sa na karasa tarwatsa kaina. Nayi kokarin juya kan amma naji yayi min nauyi ga kuma wani irin ciwo da yake min. A hankali na daga hannuna da niyyar dafe kan dan saukakawa kaina a zabar da nake ji, k kuma in toshe kunnena dan hana kaina jin kukan jaririn, amma sai naji an rike hannun nawa, sai kuma naji muryar Daddy yana magana "Safiyya? Careful kar kiji wa kan ki ciwo. Ku fita da wannan yaron daga nan dan Allah". Na dan motsa idona kadan ina jin a raina ina son in kara gain fuskar Daddy one last time, Na samu da kyar idon da yayi min nauyi ya bude, na sauke su akan Daddy da yake zaune akan kujerar sa a kusa dani hannunsa rike da nawa, ban gane inda muke ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma yayi mugun chanjawa lokaci daya yayi kamar an kara masa shekaru akan nasa, yayi ramar da ban taba gain shi da irin ta ba duk kuwa tsahon shekarun da ya dauka yana jinya. Na lura bayan shi akwai likitoci da suke tsaye a kaina blue scrub a jikin su. "Safiyya" Daddy ya sake kiran suna na "sannu! An fita da shi. Ki ci gaba da baccin ki"., Na mayar da ido na na rufe na cigaba da baccin kamar yadda ya bukata. A farkawa ta biyu ne nayi nadamar farkawar. Hoton Muhammad tare da Safina an rubuta amarya da ango a kasan hoton shine abinda ya dawo dan cikin hayyaci na, kamar yadda shine abinda ya fitar da ni daga cikin hayyacin nawa tun farko. "Muhammad!" na fada ina kokarin tashi daga kan gadon da nake kwance. Na san dai an rike ni amma ban san waye ba, naji kuma muryar Daddy sannan naji ta Aunty Hajjo, daga nan kuma naga wata maaikaciyar asibiti ta shigo da sauri ta doso ni, sannan mercifully na koma na cigaba da bacci na. Sanda na sake farwakawa ido na akan agogo ya sauka, karfe biyu da minti hudu na gani, nayi ta kallon agogon ina tunanin abinda hakan yake nufi. Biyun yaushe? Biyun kuma wacce rana? Nayi kokarin juya kaina in nemi window a dakin ko zanga hint din in safiya ce ko dare amma ban gani ba. Sai ma kaina da yake kara yi min ciwo a kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na. kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na fahimci a dakin asibiti nake, musamman saboda yanayin gadon da nake kai da kuma naurorin da suke zagaye da ni. Na duba hannuna naga drip yana shiga cikin jijiyoyina. A gefe na naga Aunty Hajjo tana kwance akan wata kujera, daga dukkan alama baccin da take ba mai nauyi bane ba. Babu Daddy a dakin. Na mayar da ido na na rufe amma kuma sai baccin yayi kaura daga cikin su, abinda ya faru ya fara dawo min a cikin kaina. Yadda rayuwata ta fara so good and perfect, lokaci daya ta juya zuwa terrible a karshe na rasa komai. Na rasa komai including my chance to marry the one person I love like crazy. Na riga na lallaba zuciyata akan ta hakura da shi, for his own sake, duk da dai har yanzu zuciyar ta wa bata gama amince wa da umarnin da na bata ba, tarin matsalolin da nake ciki sune duke danne damuwa da rashin sa, amma yanzu, after seeing his picture with Safina, komai ya dawo min sabo. Tambayar da na samu kaina da yiwa kaina ita ce "how?" Ta yaya Muhammad da Safina suka hadu a cikin watanni biyu da yan kwanaki har kuma suka yi aure? Muhammad fa? The man I thought saboda san da yake min zai jima bayan na barshi kafin yayi aure, the same man that kept telling me how he can not live without me. Then he married my sister just few months da rabuwa da ni? Ta. sister just few months da rabuwa da ni? Ta yaya zai yi min haka? Na tuno maganar Safina da take gaya min wanda zai aure ta ya turo mata friend request a social media, they get talking and he proposed yace yana son ya aure ta in few months. Hakan yana nufin Muhammad shi ya nemi Safina kenan. But why and how can he do that? Na san ya san ina da step sister mai suna Safina, na tabbatar munsha yin maganar ta dashi, so it was easy for him to find her and marry her, and dalili daya zan iya fahimta a matsayin dalilin da yasa yayi hakan, to get back at me for yaudarar sa da yake tunanin nayi. 32 17 6 A 9 8:52 PM Na mayar da ido na na rufe ina jin kaina yana kara matsanancin ciwo. And Safina. Mun sha maganar Muhammad da Safina. Abinda bani da tabbas akan sa shine idan ta san shi by face or not. Na san basu taba haduwa ba, but she must have seen his picture a waya ta, she must have. Babu yadda zata yi tace bata taba gain sa ba dan hotunan Muhammad a cikin waya ta sun fi hotuna na ni kaina yawa. Wasu hotunan ma shi kansa bai san sanda na dauke shi ba, Karya take yi tace bata gane shi ba, Duk su biyun munafukai ne Duk su biyun maciya amana ne. Duk su biyun maciya amana ne Duk su biyun kuma sai sun gane kuran su akan abinda suka yi min. I have been good, but rayuwata have turned to bad, now I am going to be bad sai in ga in da akwai riba a wannan bangaren. I am going to turn into a bad girl. I am going to destroy their marriage even if it is the last thing I will ever do. Na fara planning a kaina na yadda zanyi making life difficult for Muhammad da Safina, babu irin plan din da ban hada ba. None of which is a good thing. But to do that sai na koma Nigeria. Na fasa zama anan din kamar yadda a da na ce zanyi. Nigeria zan koma. In gasa wa Safina da Muhammad ava a hannun su. But to do that properly, I will have to get rid of cikin jikina first. Wannan mayataccen cikin a jikina. Sai a lokacin hankali na ya dawo kan cikin. Sai a lokacin tunanin da ya chunkushe a kwakwalwa ta yay giving way for feelings. And I felt empty a ciki na. Na bude ido da sauri na kalli cikin. Babu. Na daga hannuna wanda babu komai a jiki na shafa cikin, it felt weird, it felt as if bayan babyn har kayan cikina ma babu su. Naji wani relief na rabuwa da cikin ya lullube ni, sai kuma fear ta maye gurbin relief din. Ina yake? Masu adoption din sun karbe shi? Yanzu Daddy ya san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce akan hakan? san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce akan hakan? Amma kuma dazu ina bacci naji kukan jariri. It shouldn't be. Na riga nayi signing agreement cewa daga ni har dangina ba zamu ganshi ba ana cire shi za'a tafi da shi. Bana son ganin shi. Bana son duk wani abu da ya shafe shi. Wani alarm naji ya fara beefing a jikin gadon da nake. Naga Aunty Hajjo ta mike da sauri tana kallona sannan ta danna wani button da nake tunanin na kiran likitoci ne. Sai kuma ta taho inda nake ta dafa kaina. "Relax Safiyya, relax. You are alright. Everything is good. You are going to be fine". Wata nurse ta shigo da sauri tana kallon abinda yake yin karar tace "her VP is skyrocketing again" da sauri aunty Hajjo tace "then do something" ni dai ina kallon su dan ban fahimci abinda suke yi wa tashin hankali ba. Mutuwa ce fa ba wani abu ba. And mutuwa a gurina idan tazo zan kalle ta ne a matsayin mercy dan na jima ina neman ta da ma. Muryar Abdul ce ta sake tashina a karo na uku. "This baby is sooo cute Umma" Sai kuma muryar Aunty Hajjo "Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman. "Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman jagwalgwalashi kake yi. Dan ma yaron me lafiya ne ai da ba zasu barmu mu zo dashi dakin nan ba tunda preterm ne" Ya sake cewa "bara in dan kara rike shi kadan. Ai ba taba shi nake yi ba. Rike shi kawai nake yi" tayi tsaki "kai ka sani kuma. Da ka amince da abinda nace maka ai da yanzu kai zaka raini wanna jaririn. Amma kaki. Kayi wa kanka ai" yace "Umma ba fa ni naki ba, ita ce ba ta zabe ni ba" tace "bayan ka gaya mata kana da wadda kake so? Wacce mahaukaciya ce zata auri namijin da ya gaya mata yace baya son ta?" Muryar Daddy naji yayi sallama. Na juya kaina bangaren da naji muryar ta sa sannan na bude ido na a hankali na sauke su a kansa, ya turo kujerar sa kusa da gado na yana kirkiro murmushin da ni na san ba na gaskiya bane ba. "Safiyya. Kin tashi?" Ya fada yana shafa gashin kaina. "Sannu. Ya jikin ki? Me yake miki ciwo yanzu?" A hankali na bude baki da muryar da naji kamar ba tawa ba nace "Daddy. Gida zan tafi. Nigeria zan tafi" yace "okay, Okay. I will get us tickets right away, Kar ki daga hankalin ki akan hakan. Any thing you want". 14 7 8:52 PM Na dora hannu na akan cikina ina shafawa sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na dago ina kallon sa ban ce komai ba sai Sending messages is not allowed in this group. sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na dago ina kallon sa ban ce komai ba sai Aunty Hajjo ta dawo daya gefen nawa tace "jinin ki ne ya hau. Kika fadi. Aka kira ambulance suka dauko ki suka kawo ki nan. Dole aka cire babyn dan a samu damar daidaita vp din ki. Har yanzu bata zama normal ba but it is going down alhamdulillah". Daddy yana kallon ta yace "I heard she had another arrest cikin dare ko?" Aunty Hajjo ta dan yi murmushi "kar ka damu da haka Daddyn Safiyya. She will be okay insha Allah" na juya ina kallon ta sai tace "they had to admit him too. Allah ne ya kare mu. We almost lost the both of you. Whatever is worrying you Fiyya keep it aside. Nothing is worth damuwar da mahaifinki ya shiga. Ko ba kya valueing taki rayuwar I am sure ta sa matters a lot to you", Sai ta koma da baya ta karbo jaririn daga hannun Abdul shi kuma ya fita sannan ta dawo ta mika wa Daddy tace "tun jiya naga ta yar ka kake ba ku gaisa ba" ya gada hannu ya karba, na dauke kaina gefe in jin hawaye yana bin kuncina. Ba zan iya cigaba da kallon yana yin fuskar Daddy a lokacin da ya karbi babyn ba, Ko a mugun mafarki ban taba yin wanda na haifi shege ba, Ban taba yin wanda Daddy yake rike da shegen jariri daga gare ni ba. Babu abinda ba zan iya bayarwa ba a lokacin idan da zan samu Allah ya dauki raina a. idan da zan samu Allah ya dauki raina a gurin. Wannan kuma yana daga cikin dalilin da yasa na zabi bayar da jaririn. Muryar Daddy can ciki naji ace "Allahu Akbar. Allah mai kyauta da kari. Allah na gode maka. Na karbi wannan kyautar da kayi min kuma na gode maka. Allah kayi masa albarka ka bashi rayuwa mai kyau duniya da lahira" naji Aunty Hajjo tace "Ameen ya Rabbi". Sai kuma Daddy ya dan yi yar dariya yace "yanzu kai bawan Allah, upon all the people in this big wide world, ka rasa da wanda zaka yi kama sai dani?" Aunty Hajjo tayi dariya "soyayya ce yake yi maka. Kauna kai da shi har abada. Amma jarirai ba'a iya gane kamar su lokaci daya, sai sun yi wayo sosai sannan kamarsu take bayyana" Sai Daddy ya mike da jaririn a hannun sa sannan ya dora min akan cinyata, ganin bani da niyyar rike wa sai Aunty Hajjo ta taho da sauri ta rike sannan ta daga gadon da nake kai na koma kusan a zaune sai ta kwantar da shi akan cinyar ta ta saka pillow ta tare shi. Na runtse ido na ina girgiza kai na "bana son ganin shi Aunty, ki dauke shi daga jikina dan Allah" A daidai lokacin wata maaikaciyar asibitin ta shigo da takardu a hannun ta, suka gaisa da Aunty Hajjo sannan tayi bayanin cewa tana son ta cike bayanai akan jaririn da aka haifa ne for his birth certificate. Tambayar farko. ne for his birth certificate. Tambayar farko ita ce menene first name dinsa. Tayi tambayar tana kallo na, nima na bita da kallo, to in har ni zata tambaya ni kuma wa zan tambaya kenan? Daddy ne ya amsa "Adam. His first name is Adam" na juya ina kallon Daddyn. Tunda na samu cikin nan babu abinda Daddy ya tsani gani kamar cikin, abinda har ya jawo min nima baya son ganina. Ban taba tsammanin zai karbi babyn ba ballantana har ya saka masa sunan sa. Matar ta rubuta sannan ta sake next question wacce tafi komai ciwo a gurina "his surname" wanda mu a gurin mu hausawa mukan yi amfani ne da sunan uba a matsayin surname. Still ni ta sake yi wa tambayar. Sai na sunkuyar da kaina kasa hawaye yana fitowa daga ido na yana zuba akan dan jaririn da yake kan cinyata. Daddy naji ya sake amsawa again da muryar a kasa. "Adam Muhammad. His full name is Adam Adam Muhammad", Matar ta rubuta sannan ta juya ta fita. Na rufe idona ina jin hawayen yana cigaba da bin kuncina. Sai kuma na bude ido na sauke su akan dan jaririn da yake kan cinyata fuskarsa jike da hawaye na. Yar karamar fuskarsa tana kama da ta Daddy tabbas, yana kuma kama da ni. Wato dai duk a kaina ya kare. Gashi kuma ya karbi sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake. sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake zuba a kan fuskarsa ne ya saka ya motsa a hankali sannan ya bude idonsa ya sauke su a kaina. Nayi sauri na mayar da nawa idon na rufe." Aunty Hajjo dan Allah ki dauke shi daga jiki na" tazo ta saka hannu ta dauke shi sannan ta sake kwantar min da gadon tare da lullube ni. 14 11 10 8:52 PM Na rufe ido na kamar bacci zan yi, naji ta cewa Daddy zata mayar da jaririn NICU inda ake kula da shi. Sai dai tunda na rufe nawa idon idon yaron nake gani yana kallo na dasu. Ina tunanin ranar da zai kalle ni da su yace min ina ubansa. Ban san wanne kallo zaiyi min ba in nace masa ban sani ba. Ko zai fahimta? Ko kuma shima zai dora ayar tambaya a kaina kamar yadda mutane da yawa suke dorawa, including mahaifina. Sai daga baya na fahimci dalilin da yasa adoption din da nayi niyyar bayar da babyn bai tafi daidai ba. Ambulance din da aka kira ta dauke ni ba asibitin da nake ganin likita ta kai ni ba, asibiti mafi kusa kawai suka nema suka kai ni dan ceto raina. Su kuma inda aka kaini basu san waccan maganar ba, Na kuma fahimci anyi min aiki ne tun around 1pm na ranar juma'a, yanzu kuma 1pm din asabar ne, Ina jin uncle Sufyan suka shigo tare da Abdul, suka gama magana da Daddv sai. Abdul, suka gama magana da Daddy sai yazo kusa da ni yayi min sannu. Na gyada masa kai kawai ba tare da na bude ido na kalle shi ba dan ni a yanzu da naga dan da na haifa ba tare da aure ba ido da ido sai nake jin kamar nafi kowa abin kunya a duniya. Na tabbatar mutanen da suka san ni da ba zasu cigaba da yi min kallo irin wanda suke yi min da ba. Daga baya Aunty Hajjo ta dawo babu yaron a hannun ta, ta hada min ruwa a toilet ta taimaka min na tashi tsaye, sai naji kamar iska zata kada ni, na zama kamar wata tsinke. Sai da na shiga toilet sannan na kalli inda aka yanka a cikina, a mark that will forever be a reminder to me. Aunty Hajjo ta lura da abinda nake kalla tace min "kar ki damu, sun ce the scar won't be bad, sun kware a aikin su ai sosai". "It will still be there" na fada ba tare da nasan na fada ba. "Ko ba a jiki na ba the scar will forever be in my heart", Ita ta taimaka min nayi wanka yadda ba zan fama ciwona ba, ta taimaka min na shirya sannan muna fitowa ta bani abinci ta saka ni naci, banyi musu ba naci saboda ina bukatar karfin jiki na for what I have planned. Ina cikin shan kunun da ta bani ne Daddy ya sake dawowa dakin. Yana shigowa nace "Daddy ka siyo tickets din? Yaushe jirgin zai tashi?" Ya kalli Aunty Hajjo kamar mai neman taimako a gurinta, sai ta fara magana "Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki. "Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki iya yin tafiya a yana yin da kike ciki. Ki bari ki kwana biyu ayi discharging din ku daga asibiti ke da Adam Junior in yaso sai ku tafi" na ajiye cup din hannuna. "Ni na warke. Ni babu abinda yake damuna. Ni Nigeria zan tafi. Allah yau ko a kafa ne sai naje" na fara rera kuka. Daddy ya matso "Okay, okay. Bara in je in samu doctor muyi magana da shi inji. In yace zamu iya tafiya shikenan" Aunty Hajjo tace "Daddyn Safiyya ka zauna ka huta. Zan je in turo shi nan sai kuyi magana gabaki daya". Likitan yazo, bayan ya gama gwaje-gwajen sa yace zan iya tafiya tunda anfi 24 hours da yin aikin. Musamman saboda na nuna hakan na ke so su kuma suna son abinda zai faranta min ne. Sai dai jaririn yace ba za'a iya tafiya dashi ba, duk da cewa yana iya numfashi da kansa amma yana bukatar kulawar maaikatan lafiya 24/7 for at least 3 weeks kafin ay discharging din sa. Bayan ya fita muka zauna shiru ni da Daddy, sannan yace "are you sure you want to go?" Nace "Yes" yace "okay, shikenan. Zan saka ayi mana reserving next flight to Nigeria, But what about him?" Na gane wa yake nufi amma nayi shiru ban amsa ba. Ganin bana son yin maganar sai bai kara yi ba, ya dauko wayarsa ya kira ya gama settling maganar tafiyar mu sannan yace min "akwai jirgi 4:00 am zai tashi. To Lagos. Yayi?" Na gyada kai ina jujuya kofin kunun hannuna, sai ya sake cewa "and there is something I want. sake cewa "and there is something I want you to know kafin mu tafi. An daura auren ki da Mukhtar dazu" na daga kai ina kallon sa sai yayi saurin fara yi min bayani, baya son duk abinda zai bata min rai a lokacin, yace "an riga an saka lokaci. They couldn't get us on phone sai suka daura. Nima sai dazu da Abdul yaje gida ya dauko min wayata sannan na sani" banji komai ba a raina nace a hankali "it is okay Daddy". 11 10[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: Daki na na wuce da sauri na rufe kofa sannan na zube a kan carpet din gaban gadon dakin na fara rera kuka. Kukan abubuwa da yawa. Kukan da ban san ranar da zan daina shi ba alamar an bude kofar dakin an shigo, ban dago kai na ba amma a raina na san waye saboda mu biyu ne kadai a cikin gidan, besides, motsin wheelchair dinsa daban yake da motsin tafiyar sauran mutane. Ban juya na kalle shi ba amma nayi kokarin sassauta kuka na tare kuma da kokarin goge goge hawaye na. Ya jima anan a zaune yana kallo na sannan yace "I knew it. Dana na san kina nan kina kuka. But what I do not know is kukan menene kike yi? Uhmm, fada min, kukan me kike yi". Na cigaba da goge fuskata da bayan hannun rigata, ina jin yadda already fatar idon ta kumbura. Ya sake tambaya, "ina jin ki? Kukan menene kike yi?" Nace "I want you to get better. I need you to get better" yayi shiru na wani lokaci sannan yace "you know it is not going to happen. Sai kuma menene again?" Na girgiza kaina "shikenan dama. Shine kadai abinda nake yi wa kukan" yace "liar. You are also crying saboda maganar auren ki. Haka ne?" nayi shiru banyi magana ba. Ya sake tambaya ta "ba kya son auren Mukhtar? Kina so a fasa yi da shi?" Nayi shiru still ban ce komai ba. Ya zagayo kujerar sa gaba na yace "Safiyya. Ina so inyi miki aure kafin in tafi in barki. Idan na mutu na barki babu miji this people will tear you apart. Kuma dole in aura miki wanda ba za'a yi bincike ba ballantana a tono abinda ya faru da ke. Wannan ya bar ni da very limited da ke. Wannan ya bar ni da very limited options. I gave you the options. And you chose. Wanda kika zaba ba shi zuciya ta take so ba, hi zuciya ta tafi yarda da ki auri Mustapha. But you adamantly chose Mukhtar. And now you are crying. Tell me why". Na dago ido na ina kalion sa "Daddy, me yasa kake son Mustapha?" Yace "saboda a hannuna ya tashi, ni na bashi tarbiyya. Saboda mahaifiyarsa ce ta raine ki, ita ta baki tarbiyya. And sometimes family means more than blood. Sa'adatu will never harm you. But I am not so sure about Ahmad" Na dauke kaina gefe nace "you know what they want" yace "and what makes you think cewa su Ahmad ba the same thing suke so ba?" Nayi shiru ban ba shi amsa ba sai ya sake cewa "a rayuwa Safiyya, most of the relationships if not all da zaki shiga, ko ta auratayya ko business ko zamantakewa to trade by batter ake yi, to get something you have to give something. The best logic is ki san abinda mutum yake so daga gare ki, and then use that to get kema abinda kike so" Nace "Amma Daddy Mustapha fa..." Yace "he didn't do it. Ban san how many times zan gaya miki ba. He didn't do it" nayi shiru ban ce komai ba, bana son gaya wa Daddy abinda Mustapha yayi, bana son inyi using the only card din da nake amfani da shi grin taming Mustapha. Jin nayi shiru bance komai ba sai yace "are Jin nayi shiru bance komai ba sai yace "are you changing your mind or not?" Na goge hawaye na tare da girgiza kaina "no. Am not. Ina neman alfarma dai guda daya. Dan Allah Daddy bana son komawa Nigeria. I want to live here. Or somewhere else. Anywhere that is not Nigeria",. Ya juyo yana kallona, sai kuma ya juya kujerar sa yayi hanyar fita ba tare da yace min komai ba. Har ya kai bakin kofa sannan ya juyo yace min "about Mukhtar, ko da ana gobe daurin aure ne in kika chanja shawara let me know ni kuma zan tsayar da maganar". Ban amsa ba nima har ya fita, ban kuma bar space a zuciya ta da zan yi tunani akan maganar ba. Na riga na yanke shawara and I am not going back on it, duk kuwa da zafin da zuciya ta take yi min akan hakan. Yana fita waya ta ta kama kida, na san waye tun kafin ma in kalle ta dan mostly ya kan kira ni by this time. Sai dai sam bana son daukan wayar ta sa. Zuciya ta bata so. Sai nayi murmushi ina mamakin rayuwa ta, yanzu na gama ja in ja da Daddy a kan sa, akan nace shi zan aura, amma kuma still zuciyar ba son sa take yi ba. 4 8:00 PM Har ta katse ban dauka ba sai da ya sake kira sannan na dauka. Na saka wayar a kunne na banyi magana ba yace "ko baccin ne dai? Na ga alamar ke ba kya gajiya da bacci" nace "na tashi, kawai dai yau na tashi bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin bana jin dadi ne" yace "ni kuma yau cikin jin dadi na tashi. Have you heard the good news? In the next eight days you are going to be my bride. Duk da dai su Daddy suna ta insisting babu taron biki, but I want us to have ko da yar walima ne haka in kin dawo nija... .." Nace "yaya Mukhtar, I am sorry, but I don't want any walima dan Allah. And I also don't think zan dawo Nigeria." Yace "why not? Fiyya komai da ya faru ai ya wuce kuma. Daga anyi daurin auren nan shi kenan we will put everything behind us muyi facing sabuwar rayuwar mu and the ways to build a new family k0? Gashi ma Allah cikin ikonsa we will soon have a child to start the family with. Abeg, ki shafa min kansa ko kanta and tell them they are already loved at home". Abinda ya fada was supposed to made me feel better amma sai naji raina ya baci dan a lokacin bayan uban dan cikina babu abinda na tsana sama da dan cikin nawa. Amma sai na daure zuciya ta nace "kayi hakuri yaya Mukhtar. I can't. Abun zai wuce physically, but the trauma will always haunt me, and the best thing to do idan mutum yana son moving on from a traumatic experience is to change environment. Idan na dawo Nigeria ba zan iya bawa family na kulawar da suke bukata daga gare ni ba" yace "kina ganin zaki ke tunawa da shine?" Nace "not just him, Zan ke tunawa da komai" amma a raina na san babban abinda nake gudu a komawa Nigeria shine Muhammad. A yanzu da na dan saka distance a tsakanin mu gani nake kamar na samu wata kariya daga ciwon son kamar na samu wata kariya daga ciwon son sa, amma ina komawa Nigeria na san zanji tamkar an rushe katangar kariyar ne, and there is a chance na cewa zamu iya haduwa da shi, and that would be a disaster. A haka dai ya hakura ya bar ni amma bai ce ya amince ba kamar yadda Daddy ma bai ce ya amince ba, ya dai ce min zaiyi tunani a kai. Daga ranar sai na kara cigaba da lissafi na. Ina lissafa ranar aiki na kuma ina lissafa ranar daurin aure na. Safina kept calling me har sai da na daina daukan wayarta wai taji labarin daurin aure na and tana son mu shirya wani abu special ni da ita tunda muna da friends daya musamman yan secondary school din mu. Sai da taga na nuna mata bacin raina sosai sannan ta rabu da ni. Mustapha ma ya kira ni ban dauka ba, sai gashi ya turo min dogon message a Whatsapp wai yana yi min fatan alkhairi and he wants us to put everything behind us a cigaba da zumunci, and whenever I need a big brother he will be there for me. A karshe ya kara da cewa duk sanda nake bukatar a dan sassama min Mukhtar I should just give him a call. Ya rage kwana biyar daurin auren Safina ni kuma nawa shida sai ga Mommy ta kira ni. Na dauka na gaishe and she lost the words to say to me, sai kuma ta kama fada "yanzu wato da ban kira ki ba ke ba zaki taba daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kivi daukan waya ki kira ni ba ko?" Nace "kiyi hakuri Mommy" ta cigaba "na dauka a ranar da muka taho yarinyar nan a ranar zaki fara nema na amma ke ko ajikin ki ma sai kika cigaba da sabgar gabanki ko?" Nayi shiru bance komai ba, ta cigaba "ance min nan da six days za'a yi miki aiki. Kina shan magungunan ki dai ko?" Na ce "eh ina sha" amma a zahirin gaskiya rabon da insha magani tunda ta bar kasar. Tace "good. Ki kula da kanki. Ki kuma kwantar da hankalin ki, kin san a haihuwa babu abinda ake gudu irin hawan jini" na yi shiru ban ce komai ba sai ta sake cewa "ko ba ki auri Mustapha ba still ke ya ta ce" nace "Nagode Mommy". *Him* Kwanakin sauri suke tayi a gurin Gidado, so yake su tsaya, dan ya samu at least ya shaki numfashi amma sun ki tsayawa and every day there is something to do. Gidan su already har ya fara cika da mutane musamman saboda bikin biyu za'a hada, gashi kuma bikin farko ne da za'a yi a gidan na su. Wannan ya saka a dole ya rufe dakin sa ya tattara ya koma gidan sa, gidan da aka fara siya masa yanzu kuma da ya takura aka sake masa wani. 8:00 PM Babu shiri Haidar shima ya tattara nasa kayan ya bishi, duk da hakan bai yiwa Gidado dadi ba dan yaso ya samu these days to himself dan in suka kare kuma shi kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da kenan zai shiga cikin sabuwar rayuwar da bai ma san ta inda zai bullo mata ba. Yana sane yaje ya kamawa abokansa da suka zo gari musamman dan bikin hotel rooms duk kuwa da cewa akwai wanna spare gidan amma shi so yake ya zauna shi kadai. Haidar din ma sai ya bude masa part din da ya kamata ace shine nashi, shi kuma ya shiga wanda ya shirya saboda Safiyya. Ya san cewa hakan da yayi ba karamin emotional damage zai jawo wa kansa ba amma ya zabi hakan. Babu komai na furnitures a gidan dan haka sai katifu suka je dasu suka shimfida suke kwana akai, sai kuma boxes din kayan sawan da zasu yi amfani da su da sauran abubuwan da zasu bukata. Kullum da safe yake fita gurin hidimomin sa and they kept his emotions on check har sai ya dawo gida tukunna, shi farko ya dauka in ya gaji bacci zaiyi saurin daukansa kamar yadda Ya Amen ya gaya masa, amma kuma sai ya ga shi ba hakan bane ba a gare shi. Ko ya gajin, in ya kwanta sai dai yayi ta juyi, amma bacci baya zuwa idanun sai gari ya kusa wayewa. Kullum a ransa babu abinda yake yin bita sai rayuwar sa da Safiyya, babu abinda yake so irin ya fahimci abinda yayi missing, ya fahimci inda hint din cewa tana da aure yake wanda yayi missing a baya amma ya kasa gani, Except kin kai shi gidan su da tayi. She kept on delaying and delaying giving all sorts of on delaying and delaying giving all sorts of excuses. Farko excuses din nata akan cewa tana gidan uncle dinta ne kuma uncle din zai yi mata fada in ya ganta da saurayi because yana tunanin cewa bata isa yin saurayin ba, daga baya da ya fara nuna mata shi fa da gaske aure yake son yi, aurenta yake son yi, sai ta koma yi masa maganar rashin lafiyar babanta and the fact that baya zama a kasar sosai, and ranar nan da ya takura mata she said bata son ta kaishi gurin uncle dinta sai dai babanta, saboda uncle din yana son hada ta aure da dan sa Mukhtar. Ya san Mukhtar. Tun the second haduwar su da Safiyya ya san Mukhtar, kuma tun a lokacin jikinsa ya bashi cewa something was going on at least a zuciyar shi Mukhtar din, tun sanda ya ganshi din kuma yaji cewa baya son sa. Amma kuma a zuciyarsa ya san cewa kishi ne yake yi. Ya san cewa kishi yana daga cikin weaknesses din sa akan Safiyya, yana da mugun kishin da har toro yake bawa kansa sometimes, ya kuma san kishin nasa a yanzu yana daga cikin abinda yake cin zuciyarsa. The memory of her dauke da cikin wani, knowing fully well abinda ya faru kafin a samu cikin shine babban abinda yake hana mishi bacci a yanzu. A yau ma bai dawo da wuri ba sai late, hopping to fall asleep as soon as possible, yana shigowa ma da yay packing bai shiga cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan. cikin gidan ba sai ya cire dogayen kayan jikinsa ya bar singlet ya zagaya bayan gidan yana jogging da niyyar karawa kansa gajiya. A bayan ne kuma yaga wani guri da Safiyya ta saka musamman ya ware mata bai yi paving ba "spices zan shuka a gurin, akwai spices din da ba a samu sosai a kasuwa ko kuma ba za'a samu fresh one ba, to gwara in samu seeds din su in shuka da kaina in ringa using". Ya tsaya a gaban clearing din yana hakin jogging din da yake yi. "damn you. Damn you Safiyya" ya fada a fili, sannan ya wuce da sauri ya cigaba da jogging din sa. Yana cikin haka yani alamar an bude gate, ya san Haidar ne ya dawo amma kuma baya son kowa yayi masa magana a yanzu, dan haka yayi sauri yayi kwana ya shige gidan ta kofar baya ya shige dakin da yake kwana. Direct toilet ya wuce ya kunna wa kansa shower ya rufe idonsa yana jin dadin sanyin ruwan. "'Komai zafi bana iya wanka da ruwan sanyi, mura yake saka ni" Yaji muryar ta kamar a yanzu take gaya masa, Ya tuna da amsar da ya bata a lokacin, "Kar ki damu, zan koya miki ne. Ita kan ta murar sai ta hakura ta bar mu". Ya fita daga shower din ya goge jikinsa, yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din, yana kallon fuskarsa a mirror din toilet din, "Da wata farar fuskar ka anan" yayi murmushi. "Burge ki tayi" 4 8:00 PM Ya fito daga toilet din ya saka pajamas sannan ya karo karfin AC ya kashe fitila yayi addu'a ya kwanta, hoping to center his mind on something important, anything apart from Safiyya, amma babu abinda ya gani a idonsa sai Safiyya da ciki a office din sa. Babu kuma abinda yake son sani a lokacin sai abinda Safiyya take yi a wannan lokacin, babu abinda mind dinsa take saka masa sai different scenarios a abinda Safiyya take yi din. Ya mike tsaye ya kara wa kansa fanka sannan ya koma ya kwantatare da zagaye kansa da pillows, few minutes after that kuma ya sake mikewa zaune ya jawo wayarsa ya nemo number din Safina ya kira without realizing cewa karfe sha biyu ne na dare har da rabi. Sai da ta dauka sannan yayi realizing mistake din sa. "Hello Habibi. Ba ka yi bacci ba?" Ya matsar da watar daga fuskarsa yace "shit!" a hankali cikin jin haushin kansa. Sannan yace "hello? Uhmm, I think I made a mistake ba wannan number din zan kira ba" ta danyi shiru sannan tace "wa za ka kira to? By this time?" ya fara tunanin karyar da zaiyi, another of his weakness shine karya, bai iya karya ba kwata kwata. Yace "my friend, akwai wani friend dina Sahabi shi zan kira yanzu" ta sake cewa "by this time?" Yace "eh, baya bacci da wuri, nima haka" tace "ko dai ita zaka kira?" Ya dan bata rai "wa kenan?" Tace "your ex da ka fada min. Ko ita zaka kira Allah ya sa ka kira ni" ya danyi shiru sannan yace "I wish I can call her, there is nothing da ba zan iya bayarwa ba a yanzu to be able to call her. But she blocked my number. And beg me not to find another way to contact her. So to answer your question, ki kwantar da hankalin ki, ba ita zan kira ba". Tace "okay. Because I don't want to ruin the memory of the first time you call me da dare. Ba na son sunan wata ya shiga cikin memory din. It has always been a dream of mine. In ga ina waya da kai irin yadda yammata da samari suke y" yace "I told you abokina...." Tace "right. At least let me pretend ni ka kira. And since you called ya kamata mu danyi magana ai ko? At least tell me something about you da kake ganin ya kamata in sani, maybe about your friends or family ko aikin ka, anything, just talk to me " yace "okay. Let me start with the things I like, I like honesty, na tsani karya. I like tsafta a lot. Bana son hayaniya, bana son mita, bana son tsegumi ma'ana telling me something that do not concern me. And most importantly, I love my family, a lot" tace "yauwa, about the family, ban san su ba sam in banda Mufida, ita ma kuma a waya ne kadai ko hoton ta ban taba gani ba, ya kamata in san su ko?" Yace "zaki san su ai. A hankali, But the immediate family basu. al. A hankali. But the immediate family basu da yawa, daga Mama sai Abba sai Haidar and then Mufida. I am the eldest. Akwai cousins da yawa, I can't list them all. You will get to know them watarana" tace "haka ne. And your friends, aside Sahabi" yace "waye Sahabi?" Tace "Sahabi dai da zaka kira yanzu" yace "ohh that Sahabi, Sahabi my friend. Yes, akwai Sahabi and the rest. Zaki san su suma later. Now, let me call Sahabi kafin yayi bacci". Tayi ajjiyar zuciya "okay, shikenan. At least we are one step ahead. Good night Habibi". Sai dai daya ajiye wayar, maimakon ya koma ya sake gwada baccin sai ya tashi ya zauna ya dauko takarda da biro a cikin takardun da Abba ya bashi zai yi cike cike na sabon aikin da zai fara, ya juya bayan takardar kawai ya kama zane a jiki, zanen fuskar Safiyya. Sai da ya gama zana ta tas kamar zaka kira sunan ta ta amsa, sai kuma ya dukunkune takardar yayi jifa da ita ya koma ya kwanta. Da safe bai tashi da wuri ba dan baiyi bacci mai nauyi ba sai bayan sallar asuba, ya manta cewa a ranar zasu fita da Abba maganar chanjin aikin sa. He is going to take over some parts of managerial work na Company din Abba bayan bikin sa. Sai dai bai tashi ba har sai da Abban yazo gidan da kansa daukan sa kamar yadda suka shirya, ya kuma shigo har cikin gidan har dakin da yake kwance ya same shi yana bacci, takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya. takardar da ya gani a kasa ya sunkuya ya dauka ya warware. Sai ya samu guri a gefen katifar da Gidado yake kai ya zauna yana kallon zanen yarinyar da yake hannunsa. 8:00 PM Gidado yayi juyi sannan ya bude jajayen idonsa ya dora su akan Abba, sai kuma ya karasa bude don da sauri tare da mikewa zaune yana shafa fuskar sa a kokarin kore saurin baccin da yake kansa "Abba ka shigo? Ina kwana" Abba ya bishi da kallo sannan ya sake kallon takardar hannun sa. Sai lokacin Gidado ya lura da takardar, ya kara gyara zamansa yana shafa kai tare da kallon takardar da gefen ido. Abba ya nuna masa zanen tare da tambayar sa "Safiyya?" Gidado ya gyada kai bai ce komai ba. Abba ya nannade takardar ya ajiye a tsakanin su yace "ba ka son waccan yarinyar, zaka aure ta ne kawai saboda ni da mahaifiyar ka muna son kayi aure" babu alamar tambaya a cikin maganar dan haka Gidado bai bada amsa ba. Abba ya cigaba da cewa "abu na farko da na san ka riga ka sani shine we only want what's best for you. And right now, mantawa da wannan yarinyar shine the best thing for you" ya fada yana nuna zanen Safiyya with bitterness in his voice, abinda yake nun irin haushin Safiyya da yake ji a ransa. Ya cigaba da magana, "mun yanke shawarar aure shine babban abinda zai taimaka maka wajen mantawa da ita maka kayi moving forward. Sai dai daga ni har mahaifivar ka are not perfect, kuma. ni har mahaifiyar ka are not perfect, kuma bama ganin gaibu, zata iya yiwuwa abinda muka zaba maka ba shine alkhairi a gare ka ba, amma ni na san wanda yake perfect wanda kuma ya san gaibu, Allah. Ina son zan baka wani assignment, idan kayi shi dai dai zaka samu reward mai girma. Ina so kuma inyi maka wani alkawari. A cikin kwanakin nan da suka rage kafin daurin auren ka, ina so kayi istikhara, idan har kafin daurin auren ka cigaba da jin a ranka cewa still ba ka son aure to ka gaya min, ko da kwana daya ya rage zan dakatar da abin domin ya tabbata ba alkhairi bane ba. Amma idan kaji a ranka cewa ka amince kana son auren yarinyar, to sai mu cigaba da shirye shiryen mu har mu tabbatar da faruwar abin". Ya mike tsaye yana kallon sa yace "ka tashi ka shirya, your new job awaits you ", Gidado ya karbi shawarar Abba sosai, dan tun da suka yi maganar ya dukufa da yin adduoin neman zabin Allah. Babu dare babu rana. Ya kuma cigaba da shirye shiryen duk da suka kamata na bikin. Yan'uwansa sunzo na kusa da na nesa, maza da kuma mata. Da yake Abba da Mama first cousins ne sai ya zamana yan uwan duk daya ne babu banbanci, duk kuma treatment daya ake basu. Yan'uwansa samari da suka zo gari suka kuma fahimci a gidan da yaje ya boye kansa duk sai suka tattaro suka dawo gidan, sa'annin Gidado suna bangaren da yake while sa'annin Haidar suma suka tare a bangaren da yake. Gidado bai ji dadin haka ba saboda an takura masa an hana shi zama yayi hira shida zuciyarsa, shi da safiyyan shi. Sai dai kuma a wani bangaren yaji dadin hakan dan cikin kwanaki biyu kacal sai gashi yana hira da dariya sosai a cikin su. Wani lokacin idan suka nutse a cikin hira har mantawa yake yi da cewa wai aurensa ake yi, kuma wai baya son yarinyar da zai aura. Sai dai kuma yana iyakacin kokarin sa gurin danne wa dan baya son yanuwansa su fahimta har suyi ta yayata maganar a cikin dangi. Sai dai kuma yanuwan are making it extra difficult for him. Casually someone would ask him "ina yarinyar nan kuma da ka susuce akan ta kwanan baya?" His answer to that question was always "Allah yayi mata rasuwa" daga haka ba sa sake tambayar sa. In wani ma ya dauko tambayar sai a samu In wani ma ya dauko tambayar sai a samu wani ya hana shi dan kar su taba wa angon feelings din sa. Sometimes kuma su kan tambaya "wannan gidan na ka ai yafi wancan girma Gidado, me ya sa ka chanja?" And shi kuma ya kan amsa musu da cewa "amaryar ce tafi son wancan". Alhalin ita amarya ko gain gidan ba ta taba vi ba sai da masu yi mata jere suka je suka yi suka dauko mata pictures da videos. Gidan da za'a kai amaryar mai kyau ne, dan sosai iyayensa suka nuna masa gata a siyan gidan kamar yadda suke nuna masa gata a komai. Part dinsa daban na matar daban sannan a waje kuma akwai bangaren baki maza sannan da part din ma'aikatan gida (boy's quaters). A bangaren sa akwai bedrooms biyu da parlor, a nata bangaren akwai bedrooms uku da parlor. Part din bakin kuma parlor ne karami da dakuna biyu. Kamar yadda iyayen ango suka yi kokari wajen kure adakar su akan gidan Gidado haka bangaren amarya su ma suka yi nasu kokarin, dan duk dakunan da suke part dinta babu inda ba'a cika shi da kaya ba, kaya kuma na gani na fada wa da suka yi dai dai kuma suka dace da tsaruwar gidan. Abin har sai da ya bawa dangin angon mamaki, dan a binciken da suka yi wa iyayen amarya basu samu labarin cewa suna da irin wannan kudin ba, A bangaren amarya tun a week to bikin A bangaren amarya tun a week to bikin Mommy ta tafi can Katsina suka cigaba da kammala shire shiryen su, duk wani shiri da za"a yi wa amarya na gyaran jiki anyi wa Safina shi, ita kanta ta san tana da kyau, ta kuma shirya siye zuciyar angon na ta da wannan kyan nata da kuma duk kan wata kissa da kisisina da Allah ya halicci mata da ita. Ta san cewa akwai challenge a gabanta amma kuma ta shirya karbar sa hannu bibbiyu dai har zata samu muradin zuciyarta. Ta yarda da kalmar hausawa da suke cewa mahakurci mawadaci. Mommy tayi mata shirin duk da akeyi na gyaran amare dan taimaka musu wajen sauke hakkin aure da zai hau kansu, amma Mommyn ba ta san cewa ita ma da kanta Safinar ta gama siyan duk wadannan kayan har ma da wadanda suka fi na Mommyn. A shirye take tsaf da yin amfani da dukkan baiwar da Allah yayi mata wajen ganin ta mallaki Habibin na ta. 5 + 1 4:15 PM anar Lahadi ta tafi garin Abuja. A ranar ne kuma bayan kiran wayar angon sau ba adadi kamar yadda ta saba kullum ba tare da kiran ya shiga ba sai ta tura masa message. "Na shigo Abuja, Dan Allah ka zo in ganka, Ina gidan Hajiya" Sakon ya shigo masa ya karanta ya rufe ya ajiye, A ranar da ya rage saura five days daurin aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara. aure ne gidan da angon ya ke ciki ya kara cika fiye da kullum, yan uwan sa da suka 20 gari suma sun gayyato abokan su da suke gari, wasu abokan kuma sun gayyato nasu abokan. Gidan ya zama kamar wani dan karamin biki ake yi amma na maza zalla. Mama kuma ta daure musu gindi ta hanyar aiko musu da kulolin abinci kala kala. Daga nan sai hira ta balle, aka fara zancen aure da rayuwar cikinsa da challenges din sa, masu auren ciki suna baje fasahar experience din su, yayin da samari suka baje kunnuwa suna daukan darasi. Wannan ya sa angon ya zame ba tare da sun sani ba ya fice ya bar musu gidan. Sai da ya shiga motar sa kuma sannan ya fahimci bashi da gurin zuwa, dan duk friends din sa da zai iya zuwa gurin su suna cikin gidan sa, a lokacin ne sakon Safina ya sake shigowa. "Na gama abinda zanyi a Abuja. Gobe aka ce in koma. Dan Allah ka shigo". Ya rufe idonsa yana tunani for some seconds sai kuma ya bude ya kira number din ta. Tana dauka yace "gani nan zuwa" bai jira amsa ba ya katse kiran. Mintuna kadan suka kaishi kofar gidan, mai gadi ya taho da sauri da fara'a a fuskar sa amma sai Gidado ya bata rai tare da daga masa hannu alamar baya bukatar zuwan sa, sai da mai gadin ya juya sannan kuma sai yaji babu dadi a ransa tunda mutumin bai yi masa komai ba. Ya dauko wayarsa ya sake kiranta "ina waje" yace tare da sake ajiye wayar. Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye Few minutes sai gata ta fito. Jikinta sanye da hijab fuskarta babu kwalliya. Ta bude kofar gaban motar ta shiga ta zauna, sai ya dauke kansa yana jin haushin ta zauna a seat din Safiyya. Amma kuma ai shi ya kira ta. And only God knows me Safiyya take yi with her husband, why won't him enjoy himself too? Ta fara mishi magana "har na fitar da rai na dauka ba zaka zo ba. But now I am glad tunda kazo" ya juyo yana kallon ta fuskarsa a matukar daure yace "me yasa kike nemana?" Tana kallon sa tace "what's with that face? Ko nayi wani laifin ne kuma ban sani ba, I just wanted to see you kuma banga abin laifi dan ina son ganin ka ba". Yace "what's wrong with my face? I thought ita kika gani kika ce kina so" ta sunkuyar da kanta kasa fuskarta tana nuna damuwa tace "na san nina ce ina son ka ba sai ka goranta min ba. Kawai naga ranka a bace ne. Ni face din da nayi falling in love with is always happy always smiling" yace "you better get use to the unsmiling face. Because you are going to see a lot of it" suka yi shiru gabaki daya, sai da aka jima sannan da dago kai tace masa "dama nazo gari ne zanyi kunshi da saloon, and da akayi min kunshin sai na ga yayi kyau sosai, and I thought ya kamata kai zaka fara gani, I never thought hakan zai zama laifi". Yace "are you telling me kin taho tun daga Katsina zuwa Abuja kawai dan kiyi kunshi? Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu. Duk masu kunshin da suke Katsina ba zasu yi miki ba?" Ta dago kai tana kallon sa tace "actually, na fadi haka ne kawai a gida dan su barni in taho, Mommy like classy things and ta san a Abuja zan fi samun taste din ta, but in reality I just wanted to get away from her" yayi mamakin jin haka yace "why?" Tace "fada. Tun da taje Katsina take yi min fada. She is not happy with this marriage saboda bata san ka ba, she kept complaining cewa bata san sanda muka hadu ba ballantana sanda muka saba har zamu yi aure. Farko bata kasar, da tazo cewa tayi sai an daga. Da kyar ta yarda za'a yi din" tayi shiru tana jujuya hannunta sannan tace "she said you don't love me. Tace ko waya bata ga muna yi ba. There is no love vibes at all". Ya juya fusakarsa yana kallon window, sai kuma ya juyo yace "you know our agreement. And you agree with my conditions" tace "yes, I know. And ba complain nake maka ba. I just need a little bit of gesture from you. At least make it easy for me". Yace "let me ask you a question. 5 4:15 PM Why do you agree to this? Me yasa kika saka kanki a wannan situation din?" Tayi shiru tana tunani sannan tace "I love you, That is all that I know, Kuma na san I am an easy going person, bani da matsala, You may not love me know saboda yarinyar da kake so, but eventually you will fall in love. kake so, but eventually you will fall in love again. And the easiest way to make you fall in love with me is to marry you. Yanzu misali ita yarinyar da kake so din, I don't want to know her name, idan da zaka samu chance din auren ta even though bata son ka, won't you take the chance?" Yayi shiru yana tunani, sai kuma yayi sauri ya kawar da tunanin daga ransa yace "she loves me, so I can't relate to that" tace "she loves you and she left you?" Bai amsa ba sai ya dauke kansa gefe yana kara jin haushin ta, amma kuma yasan abinda ta fada gaskiya ne, shi kansa kuma a yanzu bashi da tabbas din in Safiyya tana son sa. Suka sake yin shiru a motar sannan yace "if that's all. Zan koma. I have things to do" tayi ajiyar zuciya "Okay. Nagode da ka samu damar zuwa. Ina neman alfarma amma guda daya. Please ka bari in ringa kiran ka. At least saboda hankalin Mommy ya kwanta" ya bata pan't you call someone and pretend cewa da ni kike? I am a little bit busy for phone calls" ta dago ido tana kallon sa, kawai sai yaga hawaye yana bin fuskarta, ta saka hannunta da ya sha kunshin amare yayi kyau a farar fatar ta ta goge hawayen sannan tace "okay, Na fahimta, Thank you", Ta bude kofa zata fita sai kuma yaji babu dadi a ransa yace "Safina wait" ta dakata amma bata juyo ba sai dai yana jin alamar kuka take yi yace "I am sorry, Okay, Zamu ke. kuka take yi yace "I am sorry. Okay. Zamu ke yin waya. Sai menene kuma kike so" ta juyo hawaye yana cigaba da zuba a fuskar ta tace "at least stop being mean to me. Ko baka nuna min soyayya ba ka daina wulakanta ni. It hurts a lot. You have no idea how much I have sacrificed for this relationship. The least you can do is to be nice to me". Bai sake magana ba ta fita daga motar ta rufe masa kofa. Sai da yaga ta shiga gida sannan ya tayar da motar ya tafi yana jin zuciyarsa duk tayi masa nauyi. Baya jin da din yadda yake treating yarinyar amma baya iya hana zuciyarsa gaya mata abinda yake cikin ta. Kuma kamar yadda ta fada masa, ko da bai so ta ba the least he can do is to treat her nice. Treat her kamar yadda yake treating sauran mutane, or more. Albarkacin tarin soyayyar da take yi masa. Gidan Abba ya wuce, ya tarar ana kokarin shiga sallar magrib sai ya bisu suka yi sallar itare ayan sun fito daga masallacin ya samu ya shiga ciki ya gaishe da sisters din Mama da ya gani a parlor sannan ya wuce cikin bedroom dinta ya gaishe ta itama. Har ya tashi zai tafi sai ta tambaye shi ko akwai abinda yake bukata yace a'a, sai kuma ta sake tambayar sa "ya kuke ciki da Safina kuwa? Kuna waya ma kuwa?" Ya dawo ya durkusa yana shafa kansa yace "yanzu ma daga gurinta nake. Tazo gari taje gurin kunshi" Mama tayi murmushi, yaga alamar jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to jin dadin hakan a fuskarta sannan tace "to madalla, hakan yayi kyau sosai. Allah yayi maka albarka" yace "Amen" a ransa yana jin dadin abinda tace din sosai. Tun a mota kafin ya bar gidan ya cire wayar sa daga do not disturb din da ya saka ta saboda Safina. Washegari da safe da ta kira shi sai kiran ya shiga ta sanar masa cewa zata koma shi kuma yayi mata fatan alkhairi. Da ta sauka a Katsina ma ta sake kiransa ta gaya masa cewa ta isa, yayi mata sannu, sannan reluctantly yace ta gaishe masa da Mommy. Daga nan suka fara magana, sama sama, yana replying messages dinta in ta kira kuma yana amsawa. A haka har ta turo masa hoton kunshin da aka neme shi musamman dan a nuna masa amma yaki gani, and he replied with "yayi kyau". Kamar yadda aka tsara ranar alhamis aka fara biki akayi kamun amarya a can katsina a gidan wan babanta. Mommy ta gaiyaci mutanen ta sosai sun je anyi komai da su, yan uwan ango ma an ware representatives sunje anyi kamun a gaban su a inda kuma suka samu tarba ta musamman daga gurin Mommy dan sai da ta tabbatar ta fitar da yar tata daga kunya a idon su. A 4:15 PM A ranar kuma aka shirya za'a yi kamun ango shima a nan Abuja, Sai dai kuma, tun. tun a safiyar ranar ne da samari yanuwan ango suka tashi a gidan da suke zaune tare da shi sai suka neme shi suka rasa, sai maigadin gidan ne ya gaya musu cewa tun assubar fari ya fice daga gidan a motarsa. Aka yi ta kiran wayar sa kuma bata shiga. Wasa wasa har rana ta yi sosai babu ango babu labarinsa. Tun suna boyewa suna cigaba da bincike su kadai har suka sanarwa da iyaye halin da ake ciki. Ango ya gudu. Ana ta kiran wayarsa kuma tana ta ringing amma baya dauka. Farko duk wanda aka gaya wa cewa ango ya gudu sai yayi dariya thinking cewa wasa akeyi, sai daga baya kuma sai a fahimci cewa babu wasa a cikin lamarin. Neman duniyar nan akayi wa angon aka rasa shi har lokacin kamun yayi. A gidan kakannin su aka tsara cewa za'a yi kamun. Amma rashin gain angon ya saka aka tattaro aka dawo nan gidan su angon ana ta lissafin yadda za'a yi, auntyn sa Maimoon sai dariya take yi dan ita dai ta san Muham had Gidado ba zai bata ba kamar wani key din mota, yayin da Aunty Amina ta dage sai fada take yi akan ya basu kunya sun tara mutane ya gudu ya bar su, da ya san ba zai tsaya kamun ba ai da sai ya fada musu da wuri su san abin yi. Hafsat kuwa sai kallon su kawai take yi dan dama ita bata ga amfanin kamun nan ba, daga baya dai da taga magana taki ci taki cinyewa sai ta kira Al'ameen ta zare masa ido tace sai ya fadi inda Gidado ya shiga, yayi ta rantse rantsen cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta. cewa shima wallahi bai sani ba, sai da ta fahimci da gaske yake sannan ta rabu da shi. Ana cikin haka Abba ya shigo, ya zauna yana binsu da kallo yana murmushi. Amina ta kalle shi tace tabbas yasan inda Gidado yake tunda bai nuna ya damu ba. Yace "to ni akan me zan damu? Tsakanin ku ne da shi ni babu ruwa na. In kuka kama shi duk abinda kuka ga dama kuyi masa" sai kuma ya saka hannu a aljihu ya dauko wayarsa ya kira number din Gidado, shi ya san indai da ran Gidado da kuma lafiyar sa babu yadda za'a yi ya kira shi yaki dauka. Yana kiran nasa kuwa ya dauka din, direct yace masa "kana ina?" Gidado yayi shiru kamar ba zai amsa ba sannan yace "ina daki na" yace "wanne dakin?" Yace "dakina na gidan mu". Abba yayi shiru yana jin yadda muryar Gidado tayi kasa sosai, and he can almost feel halin da zuciyar dan nasa take ciki. Yace "iyayenka suna neman ka zasu kama ka" Gidado yace "Abba ni da ba criminal ba me nayi da za'a kama ni?" Abba yace "tsakanin ku ne wannan. Ni dai yanzu ka ban amsa ta. Za'a yi ko ba za'a yi ba mu?" Daga Gidado har abban nasa sun fahimci cewa ba wai maganar kamu suke yi ba yanzu, Gidado ya sake yin shiru. Abba yace "yau kadai ta rage maka" still bai ce komai ba, Abba yace "ina jin ka" Gidado yace a hankali "za'a yi. Na amince ayi". hankali "za'a yi. Na amince ayi", Daga nan Abba ya katse wayar ya juya yana kallon yan'uwan nasa da suka saka shi a gaba suka tsare shi da ido. Ya kalli Amina yace "na ga kin damu dai da cewa sai kin jika yaron nan da nono, me zaki bani idan na gaya miki inda yake?" Tayi shiru tana tunani sai kuma tace "in dai ka gaya min inda yake daga yau zan dinga gaishe da matarka ina ce mata yaya" duk suka kwashe da dariya. Shekara da shekaru dama suna wannan rigimar tsakanin Amina da Zainab. Zainab kamar kanwa take a gurin Amina amma kuma mijinta kamar Yayan Amina ne (if you know you know ») dan haka kowa a cikin su ya dage lallai sai dayan ya bashi girma. Abba ya mike tsaye yace "yana dakin sa" sannan ya fice ya bar musu gidan. Ai kuwa Amina ta sunkuci turaren da ta taho dashi tayi dakin Gidadon sauran yan'uwa suna binta, taje kuwa tayi ta gudun kofar duniyar nan yaki budewa sai da Mammy tayi masa magana tare da yi masa alkawarin ba za'a zuba masa nono akai ba sannan yayi Ami la A bangaren Gidado ranar tun da assuba daya tashi ya yanke shawarar amsar da zai bawa Abba, Saboda shine abinda yaji hankalin sa yafi kwanciya dashi, bawai dan yaji a ransa yana son Safina ba, but yaji a ransa cewa auren shine abinda ya dace dashi, shine abinda hankalin sa ya kwanta dashi a wannan lokacin, The decision made him sad but free at the same time. Sad that he will have to made the final acceptance of the fact that Safiyya ta bar shi har abada, that his life has changed forever. Wannan yasa ya lallabo ya shigo gidan su ya shige dakin sa ba tare da kowa ya ganshi ba, making sure cewa ya boye motarsa a inda ita ma ba za'a ganta ba. Farko kwanciya yayi yayi baccin sa sai azahar ya tashi yayi sallah sannan ya kama yin aikin da yazo dakin da niyyar yi, aikin tattare duk wasu kaya nasa da duk wani abu nasa da yake da dangantaka da Safiyya, including his phone and his laptop da suke cike da hotuna da pictures dinta, ya hada su ya zuba a wata locker ya rufe. A binciken nasa ne ya dauko wata rose flower single stem da Safiyya ta taba bashi. Ya tuno lokacin da ta bashi din da kuma dalilin da ya sa yake ta ajjiye da ita. Suna tafiya ne ranar nan a hanya kamar kullum yana yi mata korafin har yanzu bata kai shi gidan su ba, kar yaje ayi mata miji a gidlan su a raba shi da ita tunda ba'a san shi she kept telling him cewa ba za'a iya raba su ba amma a karshe yace dai shi bama shi da tabbas din tana son sa da gaske ba wasa take yi masa da hankalin sa ba, suna maganar ne tayi ta tsinkar flowers a jikin bishiyoyi tana hadawa, sai da ta tara da yawa sannan ta cire ribbon din data daure gashinta da shi ta daure flowers din da shi ta bashi, tace symbol ne na son da Safiyya take wa Muhammad, Yaji dadi sosai kuma ya. take wa Muhammad. Yaji dadi sosai kuma ya karba, but He jokingly said "wannan ai gaibu ne, ana jima wa zasu yi wilting su bushe su mutu. I need something that is a forever thing. Wanda zai nuna min matsayina is a forever one a gurin ki. Something like zuwa gaishe da Daddy", A week after that, a jewelry company delivered that rose to him. Single stem ne na kyakkyawar red rose flower. An nannadeta da transparent plastic sheet. A jikin sheet din anyi rubutu da golden color in her own handwriting. Muhammad, This feeling is a forever thing. Your's Piya Amma abinda ya saka shi mamaki a lokacin shine kasancewar jewelry company ne suka yi delivering sakon. Sai da ga baya ya fahimalalili. A kasan rose din, dan box din da aka zura stem din rose din a ciki, was made of gold, pure gold molded into the shape of a heart with their initials scribbled on it "MS". It was too much of a gift da yaji a ransa cewa bai kamata yayi accepting ba, that gold is a fortune, Ya tabbatar a gida ba'a san tayi wannan kyautar ba, Amma kuma he. san tayi wanna kyautar ba. Amma kuma he so much love it da ya kasa mayar mata. Wannan ya sa ya boye ta a inda yasan babu wanda zai ganta da niyyar in sunyi aure sai ya bata abinta. But now it is never going to happen. Sai ya samu kansa da jujjuya rose din a hannun sa yana wondering me zaiyi da iya yanzu. A karshe sai ya koma kan gado ya kwanta rigingine ya dora rose din akan kirjinsa ya rufe idonsa. Yana jin wayarsa tana ta kara, kuma a ransa ya san cewa nemansa ake yi amma haka yayi ta kwanciyar sa, sai dai damuwar sa bata saka a ransa yaji cewa ya fasa yin auren ba. A haka akayi la'asar ya tashi yayi sallah ya koma ya kwanta, deciding cewa ba zai je gurin kamun sa ba. Duk wadanda suke kiransa yana gani, kuma ya yanke shawarar ba zai dauka ba. A haka har wanda ba zai iya kin daukan wayar ta sa ba ya kira shi. Ya dauka, ta tambaye shi game da decision dinsa kuma ya gaya masa amsar. Bai jima da ajiye wayar ba yaji bugun kofa da kuma muryar Aunty Amina tana mishi magana filatanci "na san kana ciki, ka bude kofar nan" ya tashi zaune yana dafe kansa, Suka cigaba da hayaniya da kuma bugun kofar. Bai ce musu komai ba sai ya tashi ya kammala adana dukkan kayan da yake bukatar adana wa including the forever rose sannan ya tsaya a bakin kofar, a lokacin yaji muryar Mammy tana masa magana, Yayi murmushi ya amsa mata da fulatanci. murmushi ya amsa mata da fulatanci. "'Amma banda nono za'a zuba min" tace "eh banda nono" yace "kinyi alkawari?" Tayi dariya tace "nayi alkawari" sannan ya bude kofar, yana budewa suka feshe shi da turaruka kala kala sannan aka dauki guda. Duk da cewa turarukan sunyi masa karfi aka, amma sai ya samu kansa da yin murmushi yana jin dadin gain iyayen nasa cikin farin ciki. 6 4:15 PM Zuwa dare sai gashi yana hira a cikin su harda dariya, ranar gabaki daya familyn anan suka ci abincin dare sannan suka raba dare suna hira, sai da bacci ya fara cin karfin sa sannan ya zame jikinsa ya koma dakinsa ya kwanta acan. Da safe ya tashi da wuri kamar yadda aka tsara ya shiga wanda, saboda da wuri zasu tafi gurin daurin auren, yana fitowa daga wanka da bathrobe a jikin sa sai ya ga Mama a zaune akan gadon sa da kayan sawa na maza a hannunta tana fesa turare a jiki. Ya rissina ya gaishe ta yana jinsa wani iri saboda bu kaya a jikinsa amma sai yaga ita ko an xinta, Ta mika masa kayan hannun ta, fuskarta dauke da alamar damuwa, tace ."ga kayan da zaka saka nan. Dan banga ka tanadi kayan sakawar yau ba" ya karba tare da yi mata godiya, bata amsa ba sai tace "kayi sauri ka shirya, baban ku har ya shirya" ya ce "to" amma sai ua cigaba da tsaiwa da kayan a hannun sa tunda dai ai ba zai saka kava a cabanta ba, zai saka kaya a gabanta ba. Ta mike a hankali kamar bata son fita. Har takai bakin kofa sai kuma ta juyo tana kallon sa tace "Muhammad?" Ya amsa, sai tace "are you happy?" Yayi shiru yana kallon damuwar da take rubuce a fuskar ta sai ya girgiza kansa yace "no, I am not happy Mama. But I am contented, alhamdulillah" tace "good. That's a good start. Allah yayi maka albarka". Sai da ta fita sannan a hankali yace "Ameen Mama" Ya shirya ya saka kayan da Mama ta bashi. Farin yadi ne tas da akayi wa aiki mai kyau kalar ruwan toka mai haske, wanda ya dace da hula da takalmin da ta ajiye masa. Ya tsaya a gaban madubi yana kallon yadda yayi kyau, shi kansa ya san yayi kyau ba kadan ba. Ya tuna maganar Safiyya "You will look so good in white" Sai yayi murmushi. "Good bye Piya". Daga nan ya juya ya fita tare da rufe kofar dakin, kna wing he will come back a changed man, al tried man. Maybe even a happy man. Abinda bai sani ba shine a yanzun ne zai bude babi mai cike da rikici da sarkakiya a rayuwar sa, Yanzun ne matsalolin zasu fara, *Her Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina. Ranakun gudu suke yi, musamman idan ina lissafa su a matsayin kwanakin da suka rage a daura min aure da Mukhtar, amma kuma lakaki suke yi idan na kalle su a matsayin ranakun da suka rage ayi min aiki a raba ni da abinda yake ciki na. Duk shire shiryen aikin sun kammala a asibitin da za'a yi, sun dauki dukkan vitals dina sun tanadi dukkan abinda suke ganin zan bukata. Sun kuma tanadi dukkan abinda babyn da za'"a ciro zai bukata tunda zai zamanto premature ne kuma zai bukaci kulawa ta musamman. Yayinda ni kuma na kammala dukkan shiryen shiryen bayar da babyn kamar yadda na riga nayi niyya. Sharuda na sune bana son ganin shi, bana son Daddy ya ganshi, bana son kuma in an samu parents din da suke son sa a basu wani information da ya shafe ni ballantana har nan gaba yayi amfani da information din gurin sanin ko ni wacece. A gida kuma kullum muna cikin rigima da Daddy, muyi rigima yayi fushi ya sauko da • kansa ko kuma ni inyi fushi ana jima wa kum sauko inje in bashi hakuri. Duk da ya amine da maganar Mukhtar amma yaki hakura da kokarin chanja min ra'ayi na. Sannu kuma har yanzu bai yarda da magana ta ta cewa ba zan koma Nigeria ba. He kept saying akwai plans din da ya shirya min in na koma Nigeria, But he wouldn't say what. Mutanen kadai da nake samun fahimtar juna da su sune twins, Kullum sai muni hirar mu a waya. Suna kuma updating dina akan duk. a waya. Suna kuma updating dina akan duk abinda yake faruwa a gidan. Su suka bani labarin rikicin da ake tayi tsakanin Mommy da Safina, a fahimtar su ita Mommy hankalin ta bai kwanta da wanda Safina zata aura ba. A kalaman ta kamar yadda suka fada min "shegen girman kai ne da shi da isa kamar wani dan sarkin Makkah" Sun so Daddy ya bar su su taho su zauna tare da mu amma yaki, ni na fahimci baya son Mommy ta sake jin haushi tace ya kwace mata su, shi lallai so yake a daidaita. Kusan kullum kuma in muna waya sai sunyi min maganar Hajiya, tana ta damn su da tambaya akai na, ta damu da ni, musamman da taji cewa za'a daura min aure. "Kin san bata san halin da kike ciki ba. Mommy bata gaya mata ba. Tace Hajiya bakinta bashi da linzami" 6 2 4:15 PM 1 '"Bata gaya mata ma maganar rikicin da suka yi da Daddy b dasan idan da ta gaya mata 'da zata iya yi yaya Safina kayan daki amma kuma da kowa a gidan bikin sai yaji labari" Nayi murmushi, a yarda da maganar Mommy a nan, Hajiya tana da kirki sosai, ammà indai magana ta shiga ta kunnen ta to sai ta fita ta bakin ta, Kuma ba wai da niyyar munafunci ba. Haka Allah yayi ta bata san wani abu wai shi sirri ba, Da ake zata san da. wani abu wai shi sirri ba. Da ake zata san da zancen cikin nan nawa, zata tausaya min sosai ta bani dukkanin kulawa, bayan ta gamai min fada, amma kuma kowa da yake gidan da wanda zai shigo gidan sai ya san maganar. Safina har da turo min pictures din gidanta sanda aka gama jerenta, sannan tayo min message din godiya. Ranar kamun ta ma haka ta turo min pictures din kyalliyar da tayi, telling me that taso ace ina nan. Sannan sai washegari, washegari ranar daurin aure. Ranar dama ban samu baccin kirki ba saboda lissafin rayuwa. Haka na gama daren akan sallaya ta. Gari yana wayewa nace saura kwana daya. Ina nan kan sallayar har lokacin in abincin Daddy yayi naje na hada masa, yanzu baya iya cin abinci mai tauri sai mai ruwa ko kuma wanda aka dafa yayi laushi sosai. Naje na kai masa na tashe shi zaune ya dauka yana ci, baya son inke bashi abinci a baki yace cin abincin da kansa ma wani exercise ne. Yana ci yake tambayata ko na gaml da kaya na na zuwa asibiti nace masa na gama, dama da yamma zan tafi, a can zan kwana. Ya sake tambayar ko akwai abinda nake bukata nace masa a'a. Ni kuma na sake yi masa maganar cewa bana son ya bini asibiti gwara yayi zamansa a gida tunda Aunty Hajjo zata je amma ya nuna min ba zai zauna a gida ba, Sometimes na kan yi tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk. tunanin a gurin sa na gado taurin kaina duk kuwa da cewa shi kullum cewa yake yi a gurin Ammi ne. Sai da nurse din shi yazo ya hada masa ruwan wanka zai taimaka masa yayi sannan na fita na koma parlor na zauna. Gaba na sai faduwa yake yi. Nayi tunanin maganar aiki na ce take damuna amma kuma ban taba damuwa da ita ba why will I now. Ina nan zaune har wajen azahar nurse din ya fito yace zai je ya dawo, ni kuma na tashi na shiga kitchen zan nema mana abinda zamu ci da rana. A lokacin ne wani tunani ya fado min. Twins sunce 11am za"a daura auren Safina. Na kalli agogo naga 12:30 ma'ana 11:30 kenan a Nigeria. Sai nayi tunanin ko an daura? Na shiga kitchen din na dora abincin sai na dawo daki nayi sallah kafin abincin ya kammala., Sai da na idar nayi adduoi na sannan na dauko waya ta zan duba ko twins sun turo min labari. Ina shiga kuwa naga méssage from Hussein. "'Yaya an daura auren Yaya Safina. We are missing you here ke da Daddy" Naji babu dadi a raina, nima ina missing din su, Sai naga ya dora status, nayi sauri na bude dan nasan pictures din daurin auren ne, A lokacin ne na ganshi, A lokacin ne na ganshi. Sai da na ajjiye wayar na saka hannayena biyu na murza idona dan in kawar da gizon da yake min, saboda kwanan nan ba a mafarki ba har a ido biyu gizo yake min in ganshi kamar ya shigo gidan ko kuma inji kamar muryarsa. Na sake daukan wayar na sake dubawa. Muhammad ne, Muhammad dina, yayi kyau fiye da yadda na taba tunanin zai yi. Yana tsaye Hussein yana tsaye shima a kusa da shi. Hussein yayi captioning hoton with "Nayi sabon wa" Menene wa? Shine tambayar da na fara yiwa kai na. Me Muhammad yake yi a gurin daurin auren Safina? Sai dai hoto na gaba shi yayi kokarin amsa min tambaya ta. Muhammad din ne dai again, this time sho da H an da Hussein. Hussein ya rubuta "With the groom. Allah ya sanya alkhairi" Naji cikina ya daure, kwakwalwa ta ta toshe. Na sake tambayar kaina "menene groom? Me kalmar groom take nufi?" Hoto na gaba ne ya hau da kansa ba tare da na tura shi ba, Muhammad ne a tsaye da Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliva cikin farin. Safina a kusa da shi. Ta ci kwalliya cikin farin lace din da na siya mata. Fuskarta dauke da tsantsar farin ciki. A kasan hoton Hussein ya rubuta. "Amarya da ango" 89 7 3 3 4:15 PM Na ajiye wayar tare da girgiza kaina kamar mai kokarin tashin kaina daga bacci, amma kuma ba baccin nake yi ba. Na dafa gadon da yake gaba na na mike ina jin kamar kaina yafi dukkan sauran jiki na girma saboda kamar dukkan jinin jikina ya tattare ya koma cikin kan, shi kansa bugun zuciya ta a cikin kai na nake jin sa. In dai har da gaske ba mafarki nake yi ba, ba kuma haukacewa nayi nake hallucinations ba, to tabbas auren Safina da Muhammad Gidado aka daura shi. Na dafa bango na fara kokarin fita waje sai, kuma na dawo dakin na dauki handbag dina da take ajjiye akan side drawer na rataya, na cigaba da laluben hanya har na fita parlor. "Daday!" Na fada da karfin da bansan ina da shi ba. Na cigaba da tafiya ina gain gaba na yana kara duhu duk kuwa da ba dare ne yayi ba, Sama sama naji muryar Daddy yana magana, "Safiyya! Lafiyar ki, Me ya faru? Ina zaki je" na juyo inda naji sautin muryarsa nace "gida zanje, Nigeria zan tafi, Daddy Muhammad ne fa, Wallahi Daddy shine. Muhammad ne fa. Wallahi Daddy shine. Daddy mutuwa zanyi. Daddy zuciya ta zata fashe. Daddy mutuwa zany" na cigaba da fadar sauran maganganun da ban san me nake cewa ba yayin da jiri ya debe ni nayi kasa. Dishi dashi naga motsin Daddy ya mike daga kan wheelchair dinsa yayo kaina, sai dai kafin ya karaso ya yanke jiki ya riga ni kaiwa kasa. Sai da kaina ya daki center table din gurin sannan ya karasa kasa. Na hango Daddy ya sake yunkurawa zuwa inda nake fuskarsa da cike da tashin hankali. "Not my daughter. God please take me instead" ya fada a hankali. Sannan kuma da karfi yace "who is there? help us please. Help!" A hankali na sake ce masa "Daddy Muhammad ne". Sannan na rufe ido na into nothingness.... Longest episode ever Shin kina son wannan episode din ya zamar miki taliyar karshe ko kina son kari....... .... Muhammad dai ya auri Safina, while madly in love with Safiyya, ba tare da yasan. Shin kina son wannan episode din ya zamar miki taliyar karshe ko kina son kari.......... Muhammad dai ya auri Safina, while madly in love with Safiyya, ba tare da yasan dangantakar dake tsakanin Safina da Safiyya ba. Ga Safiyya kuma ta dauki hanyar lahira bamu sani ba ko zata yi rai ko akasin haka. In bata tafi lahirar ba ma she is set to marry Mukhtar Yaya wanna badakalar zata kare Yaya wadannan aurarraki zasu kasance. Menene ainahin labarin Safiyya da mahaifiyar ta Menene dangantakar su da Mommy And above all, wanene uban cikin jikin Safiyya. Kina son wadannan amsoshin? Na tabbatar kina so, Turo naira 500 dinki zuwa wannan account din 0779484.494 Nafisa Tafida Usman Access Bank - Safiyya' owner 8:51 PM Episode Sixteen: Junior Kukan jariri ne sound din da ya fara ratsa consciousness dina, kamar a cikin kai na aka saka min jaririn, kamar a cikin kwakwalwa ta yake kukan cikin kokarin sa na karasa tarwatsa kaina. Nayi kokarin juya kan amma naji yayi min nauyi ga kuma wani irin ciwo da yake min. A hankali na daga hannuna da niyyar dafe kan dan saukakawa kaina a zabar da nake ji, k kuma in toshe kunnena dan hana kaina jin kukan jaririn, amma sai naji an rike hannun nawa, sai kuma naji muryar Daddy yana magana "Safiyya? Careful kar kiji wa kan ki ciwo. Ku fita da wannan yaron daga nan dan Allah". Na dan motsa idona kadan ina jin a raina ina son in kara gain fuskar Daddy one last time, Na samu da kyar idon da yayi min nauyi ya bude, na sauke su akan Daddy da yake zaune akan kujerar sa a kusa dani hannunsa rike da nawa, ban gane inda muke ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma ba amma na gane Daddy na, sai dai kuma yayi mugun chanjawa lokaci daya yayi kamar an kara masa shekaru akan nasa, yayi ramar da ban taba gain shi da irin ta ba duk kuwa tsahon shekarun da ya dauka yana jinya. Na lura bayan shi akwai likitoci da suke tsaye a kaina blue scrub a jikin su. "Safiyya" Daddy ya sake kiran suna na "sannu! An fita da shi. Ki ci gaba da baccin ki"., Na mayar da ido na na rufe na cigaba da baccin kamar yadda ya bukata. A farkawa ta biyu ne nayi nadamar farkawar. Hoton Muhammad tare da Safina an rubuta amarya da ango a kasan hoton shine abinda ya dawo dan cikin hayyaci na, kamar yadda shine abinda ya fitar da ni daga cikin hayyacin nawa tun farko. "Muhammad!" na fada ina kokarin tashi daga kan gadon da nake kwance. Na san dai an rike ni amma ban san waye ba, naji kuma muryar Daddy sannan naji ta Aunty Hajjo, daga nan kuma naga wata maaikaciyar asibiti ta shigo da sauri ta doso ni, sannan mercifully na koma na cigaba da bacci na. Sanda na sake farwakawa ido na akan agogo ya sauka, karfe biyu da minti hudu na gani, nayi ta kallon agogon ina tunanin abinda hakan yake nufi. Biyun yaushe? Biyun kuma wacce rana? Nayi kokarin juya kaina in nemi window a dakin ko zanga hint din in safiya ce ko dare amma ban gani ba. Sai ma kaina da yake kara yi min ciwo a kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na. kokarin juya shi da nake yi. A lokacin na fahimci a dakin asibiti nake, musamman saboda yanayin gadon da nake kai da kuma naurorin da suke zagaye da ni. Na duba hannuna naga drip yana shiga cikin jijiyoyina. A gefe na naga Aunty Hajjo tana kwance akan wata kujera, daga dukkan alama baccin da take ba mai nauyi bane ba. Babu Daddy a dakin. Na mayar da ido na na rufe amma kuma sai baccin yayi kaura daga cikin su, abinda ya faru ya fara dawo min a cikin kaina. Yadda rayuwata ta fara so good and perfect, lokaci daya ta juya zuwa terrible a karshe na rasa komai. Na rasa komai including my chance to marry the one person I love like crazy. Na riga na lallaba zuciyata akan ta hakura da shi, for his own sake, duk da dai har yanzu zuciyar ta wa bata gama amince wa da umarnin da na bata ba, tarin matsalolin da nake ciki sune duke danne damuwa da rashin sa, amma yanzu, after seeing his picture with Safina, komai ya dawo min sabo. Tambayar da na samu kaina da yiwa kaina ita ce "how?" Ta yaya Muhammad da Safina suka hadu a cikin watanni biyu da yan kwanaki har kuma suka yi aure? Muhammad fa? The man I thought saboda san da yake min zai jima bayan na barshi kafin yayi aure, the same man that kept telling me how he can not live without me. Then he married my sister just few months da rabuwa da ni? Ta. sister just few months da rabuwa da ni? Ta yaya zai yi min haka? Na tuno maganar Safina da take gaya min wanda zai aure ta ya turo mata friend request a social media, they get talking and he proposed yace yana son ya aure ta in few months. Hakan yana nufin Muhammad shi ya nemi Safina kenan. But why and how can he do that? Na san ya san ina da step sister mai suna Safina, na tabbatar munsha yin maganar ta dashi, so it was easy for him to find her and marry her, and dalili daya zan iya fahimta a matsayin dalilin da yasa yayi hakan, to get back at me for yaudarar sa da yake tunanin nayi. 32 17 6 A 9 8:52 PM Na mayar da ido na na rufe ina jin kaina yana kara matsanancin ciwo. And Safina. Mun sha maganar Muhammad da Safina. Abinda bani da tabbas akan sa shine idan ta san shi by face or not. Na san basu taba haduwa ba, but she must have seen his picture a waya ta, she must have. Babu yadda zata yi tace bata taba gain sa ba dan hotunan Muhammad a cikin waya ta sun fi hotuna na ni kaina yawa. Wasu hotunan ma shi kansa bai san sanda na dauke shi ba, Karya take yi tace bata gane shi ba, Duk su biyun munafukai ne Duk su biyun maciya amana ne. Duk su biyun maciya amana ne Duk su biyun kuma sai sun gane kuran su akan abinda suka yi min. I have been good, but rayuwata have turned to bad, now I am going to be bad sai in ga in da akwai riba a wannan bangaren. I am going to turn into a bad girl. I am going to destroy their marriage even if it is the last thing I will ever do. Na fara planning a kaina na yadda zanyi making life difficult for Muhammad da Safina, babu irin plan din da ban hada ba. None of which is a good thing. But to do that sai na koma Nigeria. Na fasa zama anan din kamar yadda a da na ce zanyi. Nigeria zan koma. In gasa wa Safina da Muhammad ava a hannun su. But to do that properly, I will have to get rid of cikin jikina first. Wannan mayataccen cikin a jikina. Sai a lokacin hankali na ya dawo kan cikin. Sai a lokacin tunanin da ya chunkushe a kwakwalwa ta yay giving way for feelings. And I felt empty a ciki na. Na bude ido da sauri na kalli cikin. Babu. Na daga hannuna wanda babu komai a jiki na shafa cikin, it felt weird, it felt as if bayan babyn har kayan cikina ma babu su. Naji wani relief na rabuwa da cikin ya lullube ni, sai kuma fear ta maye gurbin relief din. Ina yake? Masu adoption din sun karbe shi? Yanzu Daddy ya san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce akan hakan? san na bayar da shi kenan? Me Daddy zai ce akan hakan? Amma kuma dazu ina bacci naji kukan jariri. It shouldn't be. Na riga nayi signing agreement cewa daga ni har dangina ba zamu ganshi ba ana cire shi za'a tafi da shi. Bana son ganin shi. Bana son duk wani abu da ya shafe shi. Wani alarm naji ya fara beefing a jikin gadon da nake. Naga Aunty Hajjo ta mike da sauri tana kallona sannan ta danna wani button da nake tunanin na kiran likitoci ne. Sai kuma ta taho inda nake ta dafa kaina. "Relax Safiyya, relax. You are alright. Everything is good. You are going to be fine". Wata nurse ta shigo da sauri tana kallon abinda yake yin karar tace "her VP is skyrocketing again" da sauri aunty Hajjo tace "then do something" ni dai ina kallon su dan ban fahimci abinda suke yi wa tashin hankali ba. Mutuwa ce fa ba wani abu ba. And mutuwa a gurina idan tazo zan kalle ta ne a matsayin mercy dan na jima ina neman ta da ma. Muryar Abdul ce ta sake tashina a karo na uku. "This baby is sooo cute Umma" Sai kuma muryar Aunty Hajjo "Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman. "Da Allah ajiye shi haka nan. Sai faman jagwalgwalashi kake yi. Dan ma yaron me lafiya ne ai da ba zasu barmu mu zo dashi dakin nan ba tunda preterm ne" Ya sake cewa "bara in dan kara rike shi kadan. Ai ba taba shi nake yi ba. Rike shi kawai nake yi" tayi tsaki "kai ka sani kuma. Da ka amince da abinda nace maka ai da yanzu kai zaka raini wanna jaririn. Amma kaki. Kayi wa kanka ai" yace "Umma ba fa ni naki ba, ita ce ba ta zabe ni ba" tace "bayan ka gaya mata kana da wadda kake so? Wacce mahaukaciya ce zata auri namijin da ya gaya mata yace baya son ta?" Muryar Daddy naji yayi sallama. Na juya kaina bangaren da naji muryar ta sa sannan na bude ido na a hankali na sauke su a kansa, ya turo kujerar sa kusa da gado na yana kirkiro murmushin da ni na san ba na gaskiya bane ba. "Safiyya. Kin tashi?" Ya fada yana shafa gashin kaina. "Sannu. Ya jikin ki? Me yake miki ciwo yanzu?" A hankali na bude baki da muryar da naji kamar ba tawa ba nace "Daddy. Gida zan tafi. Nigeria zan tafi" yace "okay, Okay. I will get us tickets right away, Kar ki daga hankalin ki akan hakan. Any thing you want". 14 7 8:52 PM Na dora hannu na akan cikina ina shafawa sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na dago ina kallon sa ban ce komai ba sai Sending messages is not allowed in this group. sai ya rike hannun "kar ki taba ciwon" na dago ina kallon sa ban ce komai ba sai Aunty Hajjo ta dawo daya gefen nawa tace "jinin ki ne ya hau. Kika fadi. Aka kira ambulance suka dauko ki suka kawo ki nan. Dole aka cire babyn dan a samu damar daidaita vp din ki. Har yanzu bata zama normal ba but it is going down alhamdulillah". Daddy yana kallon ta yace "I heard she had another arrest cikin dare ko?" Aunty Hajjo ta dan yi murmushi "kar ka damu da haka Daddyn Safiyya. She will be okay insha Allah" na juya ina kallon ta sai tace "they had to admit him too. Allah ne ya kare mu. We almost lost the both of you. Whatever is worrying you Fiyya keep it aside. Nothing is worth damuwar da mahaifinki ya shiga. Ko ba kya valueing taki rayuwar I am sure ta sa matters a lot to you", Sai ta koma da baya ta karbo jaririn daga hannun Abdul shi kuma ya fita sannan ta dawo ta mika wa Daddy tace "tun jiya naga ta yar ka kake ba ku gaisa ba" ya gada hannu ya karba, na dauke kaina gefe in jin hawaye yana bin kuncina. Ba zan iya cigaba da kallon yana yin fuskar Daddy a lokacin da ya karbi babyn ba, Ko a mugun mafarki ban taba yin wanda na haifi shege ba, Ban taba yin wanda Daddy yake rike da shegen jariri daga gare ni ba. Babu abinda ba zan iya bayarwa ba a lokacin idan da zan samu Allah ya dauki raina a. idan da zan samu Allah ya dauki raina a gurin. Wannan kuma yana daga cikin dalilin da yasa na zabi bayar da jaririn. Muryar Daddy can ciki naji ace "Allahu Akbar. Allah mai kyauta da kari. Allah na gode maka. Na karbi wannan kyautar da kayi min kuma na gode maka. Allah kayi masa albarka ka bashi rayuwa mai kyau duniya da lahira" naji Aunty Hajjo tace "Ameen ya Rabbi". Sai kuma Daddy ya dan yi yar dariya yace "yanzu kai bawan Allah, upon all the people in this big wide world, ka rasa da wanda zaka yi kama sai dani?" Aunty Hajjo tayi dariya "soyayya ce yake yi maka. Kauna kai da shi har abada. Amma jarirai ba'a iya gane kamar su lokaci daya, sai sun yi wayo sosai sannan kamarsu take bayyana" Sai Daddy ya mike da jaririn a hannun sa sannan ya dora min akan cinyata, ganin bani da niyyar rike wa sai Aunty Hajjo ta taho da sauri ta rike sannan ta daga gadon da nake kai na koma kusan a zaune sai ta kwantar da shi akan cinyar ta ta saka pillow ta tare shi. Na runtse ido na ina girgiza kai na "bana son ganin shi Aunty, ki dauke shi daga jikina dan Allah" A daidai lokacin wata maaikaciyar asibitin ta shigo da takardu a hannun ta, suka gaisa da Aunty Hajjo sannan tayi bayanin cewa tana son ta cike bayanai akan jaririn da aka haifa ne for his birth certificate. Tambayar farko. ne for his birth certificate. Tambayar farko ita ce menene first name dinsa. Tayi tambayar tana kallo na, nima na bita da kallo, to in har ni zata tambaya ni kuma wa zan tambaya kenan? Daddy ne ya amsa "Adam. His first name is Adam" na juya ina kallon Daddyn. Tunda na samu cikin nan babu abinda Daddy ya tsani gani kamar cikin, abinda har ya jawo min nima baya son ganina. Ban taba tsammanin zai karbi babyn ba ballantana har ya saka masa sunan sa. Matar ta rubuta sannan ta sake next question wacce tafi komai ciwo a gurina "his surname" wanda mu a gurin mu hausawa mukan yi amfani ne da sunan uba a matsayin surname. Still ni ta sake yi wa tambayar. Sai na sunkuyar da kaina kasa hawaye yana fitowa daga ido na yana zuba akan dan jaririn da yake kan cinyata. Daddy naji ya sake amsawa again da muryar a kasa. "Adam Muhammad. His full name is Adam Adam Muhammad", Matar ta rubuta sannan ta juya ta fita. Na rufe idona ina jin hawayen yana cigaba da bin kuncina. Sai kuma na bude ido na sauke su akan dan jaririn da yake kan cinyata fuskarsa jike da hawaye na. Yar karamar fuskarsa tana kama da ta Daddy tabbas, yana kuma kama da ni. Wato dai duk a kaina ya kare. Gashi kuma ya karbi sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake. sunan Daddy. Ruwan hawayen nawa da yake zuba a kan fuskarsa ne ya saka ya motsa a hankali sannan ya bude idonsa ya sauke su a kaina. Nayi sauri na mayar da nawa idon na rufe." Aunty Hajjo dan Allah ki dauke shi daga jiki na" tazo ta saka hannu ta dauke shi sannan ta sake kwantar min da gadon tare da lullube ni. 14 11 10 8:52 PM Na rufe ido na kamar bacci zan yi, naji ta cewa Daddy zata mayar da jaririn NICU inda ake kula da shi. Sai dai tunda na rufe nawa idon idon yaron nake gani yana kallo na dasu. Ina tunanin ranar da zai kalle ni da su yace min ina ubansa. Ban san wanne kallo zaiyi min ba in nace masa ban sani ba. Ko zai fahimta? Ko kuma shima zai dora ayar tambaya a kaina kamar yadda mutane da yawa suke dorawa, including mahaifina. Sai daga baya na fahimci dalilin da yasa adoption din da nayi niyyar bayar da babyn bai tafi daidai ba. Ambulance din da aka kira ta dauke ni ba asibitin da nake ganin likita ta kai ni ba, asibiti mafi kusa kawai suka nema suka kai ni dan ceto raina. Su kuma inda aka kaini basu san waccan maganar ba, Na kuma fahimci anyi min aiki ne tun around 1pm na ranar juma'a, yanzu kuma 1pm din asabar ne, Ina jin uncle Sufyan suka shigo tare da Abdul, suka gama magana da Daddv sai. Abdul, suka gama magana da Daddy sai yazo kusa da ni yayi min sannu. Na gyada masa kai kawai ba tare da na bude ido na kalle shi ba dan ni a yanzu da naga dan da na haifa ba tare da aure ba ido da ido sai nake jin kamar nafi kowa abin kunya a duniya. Na tabbatar mutanen da suka san ni da ba zasu cigaba da yi min kallo irin wanda suke yi min da ba. Daga baya Aunty Hajjo ta dawo babu yaron a hannun ta, ta hada min ruwa a toilet ta taimaka min na tashi tsaye, sai naji kamar iska zata kada ni, na zama kamar wata tsinke. Sai da na shiga toilet sannan na kalli inda aka yanka a cikina, a mark that will forever be a reminder to me. Aunty Hajjo ta lura da abinda nake kalla tace min "kar ki damu, sun ce the scar won't be bad, sun kware a aikin su ai sosai". "It will still be there" na fada ba tare da nasan na fada ba. "Ko ba a jiki na ba the scar will forever be in my heart", Ita ta taimaka min nayi wanka yadda ba zan fama ciwona ba, ta taimaka min na shirya sannan muna fitowa ta bani abinci ta saka ni naci, banyi musu ba naci saboda ina bukatar karfin jiki na for what I have planned. Ina cikin shan kunun da ta bani ne Daddy ya sake dawowa dakin. Yana shigowa nace "Daddy ka siyo tickets din? Yaushe jirgin zai tashi?" Ya kalli Aunty Hajjo kamar mai neman taimako a gurinta, sai ta fara magana "Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki. "Safiyya, kema kin san babu yadda za'a yi ki iya yin tafiya a yana yin da kike ciki. Ki bari ki kwana biyu ayi discharging din ku daga asibiti ke da Adam Junior in yaso sai ku tafi" na ajiye cup din hannuna. "Ni na warke. Ni babu abinda yake damuna. Ni Nigeria zan tafi. Allah yau ko a kafa ne sai naje" na fara rera kuka. Daddy ya matso "Okay, okay. Bara in je in samu doctor muyi magana da shi inji. In yace zamu iya tafiya shikenan" Aunty Hajjo tace "Daddyn Safiyya ka zauna ka huta. Zan je in turo shi nan sai kuyi magana gabaki daya". Likitan yazo, bayan ya gama gwaje-gwajen sa yace zan iya tafiya tunda anfi 24 hours da yin aikin. Musamman saboda na nuna hakan na ke so su kuma suna son abinda zai faranta min ne. Sai dai jaririn yace ba za'a iya tafiya dashi ba, duk da cewa yana iya numfashi da kansa amma yana bukatar kulawar maaikatan lafiya 24/7 for at least 3 weeks kafin ay discharging din sa. Bayan ya fita muka zauna shiru ni da Daddy, sannan yace "are you sure you want to go?" Nace "Yes" yace "okay, shikenan. Zan saka ayi mana reserving next flight to Nigeria, But what about him?" Na gane wa yake nufi amma nayi shiru ban amsa ba. Ganin bana son yin maganar sai bai kara yi ba, ya dauko wayarsa ya kira ya gama settling maganar tafiyar mu sannan yace min "akwai jirgi 4:00 am zai tashi. To Lagos. Yayi?" Na gyada kai ina jujuya kofin kunun hannuna, sai ya sake cewa "and there is something I want. sake cewa "and there is something I want you to know kafin mu tafi. An daura auren ki da Mukhtar dazu" na daga kai ina kallon sa sai yayi saurin fara yi min bayani, baya son duk abinda zai bata min rai a lokacin, yace "an riga an saka lokaci. They couldn't get us on phone sai suka daura. Nima sai dazu da Abdul yaje gida ya dauko min wayata sannan na sani" banji komai ba a raina nace a hankali "it is okay Daddy". 11 10 [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: "and there is something I want. sake cewa "and there is something I want you to know kafin mu tafi. An daura auren ki da Mukhtar dazu" na daga kai ina kallon sa sai yayi saurin fara yi min bayani, baya son duk abinda zai bata min rai a lokacin, yace "an riga an saka lokaci. They couldn't get us on phone sai suka daura. Nima sai dazu da Abdul yaje gida ya dauko min wayata sannan na sani" banji komai ba a raina nace a hankali "it is okay Daddy". 11 10 8:52 PM Aunty Hajjo ce da Abdul suka koma gidan da muke suke dauko mana kayan mu da suke ganin zamu tafi dasu, sannan kuma ta cigaba da zama a tare da ni kafin lokacin da zamu tafi airport yayi. A cikin lokacin ne ta koma NICU ta kuma dauko jaririn ta dawo min dashi gurina ta sake dora min shi akan cinyata sannan ta kuma yi min tambayar da Daddy yayi min dazu "sun ce ba za'a iya tafiva da shi ba. What do you intend to do with him?" Na sauke idona kasa ina kallon sa, ya na ta baccin sa ya turo dan karamin harshen sa waje yana tsotsa, na saka dan yatsa na shafa gefen fuskar sa inajin abinda ban taba tunanin zanji ba, abinda tsoron sa ya saka nayi niyyar bada shi ba tare da na ganshi ba. Aunty Hajjo ta zauna a gefe na tana kallon babyn ita ma tace "he is your son Safiyya. He is your responsibility now. He is now totally dependent on you. Dole ki zama strong, even if not for your daddy but for vour son". strong, even if not for your daddy but for your son". Ya dago dan karamin hannunsa cikin bacci ya rike dan yatsa na da na dora a fuskar sa ya cigaba da baccin sa. Naji hawaye na ya dawo. Wannan innocent halittar yanzu ta zama alhaki na, alhakin kulawa da shi da komai na sa yana hannuna a yanzu. Duk wani decision da zanyi will affect him positively or negatively. Naji a raina cewa na gama finalizing shawara ta. Na daga kai ina kallon Aunty Hajjo nace "I wanted to give him out. Har nayi signing him up for adoption a wancan asibitin" ta bude ido da mamaki amma kuma sai ta rufe da alama bata son tayi judging dina, nace "yes, that was a pretty dumb decision. I wasn't thinking right, har yanzu ma tunani na ba shi da kyau. Emotions dina are not on check. But still I don't think the right place for him is with me in Nigeria, at least not for now. Zuwa da shi gida zai wargaza duk abinda Daddy yayi sacrificing a lot to cover up. And in Nigeria people will always tag him as a bastard. The tag will follow him up har karshen rayuwar sa". Ya bude idonsa yana kallona kamar yadda nima nake kallon sa ina jin wani nauyi a zuciyata, Sai kuma na daga kai na kalli Aunty Hajjo nace "Aunty kin bani wani labari kwanan baya, labarin yadda kika so ki dauke ni ki rike ni kamar yar ki a lokacin da Ammi ta mutu, I don't know if you still have wannan burin a ranki" tayi shiru bata ce min komai. bata son tayi judging dina, nace "yes, that was a pretty dumb decision. I wasn't thinking right, har yanzu ma tunani na ba shi da kyau. Emotions dina are not on check. But still I don't think the right place for him is with me in Nigeria, at least not for now. Zuwa da shi gida zai wargaza duk abinda Daddy yayi sacrificing a lot to cover up. And in Nigeria people will always tag him as a bastard. The tag will follow him up har karshen rayuwar sa". Ya bude idonsa yana kallona kamar yadda nima nake kallon sa ina jin wani nauyi a zuciyata. Sai kuma na daga kai na kalli Aunty Hajjo nace "Aunty kin bani wani labari kwanan baya, labarin yadda kika so ki dauke ni ki rike ni kamar yar ki a lokacin da Ammi ta mutu, I don't know if you still have wannan burin a ranki" tayi shiru bata ce min komai ba sai na daga jaririn na mika mata "ban sani ba ko zaki iya cika wannan burin akan Junior? No one will know he is not yours a Nigeria. At least not for now, Sanda zai san gaskiya he will be old enough and strong enough to understand". EPISODE SEVENTEEN owner 0 11 7:39 PM Safiyya LTE 0 Episode Seventeen: The Wedding Crasher Paid advert Akwai 10% discount ga first 10 people da suka fara ordering a cikin mutanen maman Maama Contact her on 08033308307 Ki gyara rayuwar aurenki tare da amfani da ingantattun magunguna mata masu Kara lafiya da kuzari ga rayuwar ma'aurata. Mun tsaya mun tantance mun zabo muku herbs da Kuma spice da suke enhancing sexually wellness dinku. Kina fama da sanyi Kuma kinyi magani yaki tafiya? Gwada maganin mu (INFECTION CURE SET)na sanyi kiga iKon Allah,sanyi ko yasa kin bude in shaa Allah in kika yi amfani da maganin mu zaki samu waraka. Haka Kuma dan kina bugatar wadatacciyar niima da zaki tashi kan yallabai to ki Nemo WETNESS PRODUCT dinmu. In Kuma dandano kike so hajiya gidan kika. to ki Nemo WETNESS PRODUCT dinmu. In Kuma dandano kike so hajiya gidan kika zo, muna da SWEETNESS SET kiga aiki da cikawa. Akwai POST-PARTUM SET a masu jego,akwai BRIDAL SET na amare. *Sannan ga masu son sarin kayanmu muna da starter kit na magungunan da zaki siyar ki samu alkhairi a ciki, kin huta da 'yar murya akan 50k kacal* Elevate your intimacy and ignite your passion with our expert advice and carefully curated products. Your journey to enhanced sexual wellness starts here. Tayi shiru tana kallona sannan ta kalli dan jaririn da nake mika mata. Ta jima tana neman haihuwa, tun daga Abdul bata sake haihuwa ba dan tare suka yi ta neman haihuwa ita da Ammi kafin a haife ni. Har daga baya ta hakura ta saka a ranta cewa da daya Allah ya rubuta mata zata samu. Tabbas tana da shekaru amma kuma ba abin da ya kamata ayi mamaki bane ba idan ta haihu. Tunda in rear occasions mata masu irin shekarunta su kan haihu. Sannan kuma tafi shekaru uku rabon ta da Nigeria, kuma tafi shekara rabon da wani daya santa a gida ya kawo mata ziyara Berlin. Sai mu da muka zo yanzu. Dan haka abu ne mai matukar sauki tayi passing junior as her son kuma. sauki tayi passing junior as her son kuma babu wanda zai musa. Wannan zai baya Junior kariya daga zagi da tozarcin mutanen mu na kasancewarsa marar ba. Idan lokacin da ya kamata ya sani kuma yayi, shi kadai ne ya kamata ya sani din tunda duk wadanda abin zai shafa already sun riga sun sani. Ta miko hannu a hankali ta karbe shi, muryarta kamar zata yi kuka tace "I don't know what to say" nace "you don't have to say anything. Except in kina ganin it's too much of a burden" na fada ina mika mata hannu na dan lokaci daya kuma naji kamar ba zan iya rabuwa da shi ba. Ta matsa baya tana rungume shi a kirjinta tace "he will never be a burden. Kamar kuma yadda kika fada, barin shi a gurin mu is the best thing to do to him a yanzu. Allah ya bamu ikon rike shi da amana. Ke kuma Allah yayi miki jagora a dukkan sauran al'amuran da zaki fuskanta"., Na sauke hannayena kasa ina ji na empty, sai kuma a hankali nace "Ameen". Bayan nan ne na gaya wa Daddy shawarar da na yanke akan Junior, he was first concern cewa kar mu takura musu mu hada su da rainon jaririn da basu haifa ba, amma bayan yayi magana da uncle Sufyan da da aunty Hajjo sai naga ya samu relief, Dan ya fahimci ma su murna suke yi da samun abinda suka jima suna nema. Sai 3am muka bar asibitin, bayan likita ya sake duba ni tare da bani duk shawarwarin. sake duba ni tare da bani duk shawarwarin da ya kamata ya bani, most of which ta kunnen dama na suke shiga suna fita ta kunnen hagu. Sai da suka gama sannan suka rubuta mana takardar sallama ni da Daddy, suka kuma rubuta mana report din da zamu bawa doctor din mu a Nigeria yadda zai cigaba da kula da lafiyar mu. Ya ja mana kunne duk mu biyun akan gudun abinda zai ke tayar mana da hankali, ya kuma bamu shawara da mu kula da junan mu. Kafin mu bar asibitin na biya ta NICU, naje har gaban dan akwatin da aka kwantar da junior na daga ina kallon yar karamar fuskarsa ta bakwaini, sannan na saka dan yatsa na shafa fuskarsa nace "goodbye Adam" yayi mika ya bude ido ya kalle ni sannan ya cigaba da baccin sa. 23 15 4 A 2 7:46 PM By 4am muna cikin jirgi, by 5 already munyi nisa a tafiyar mu. The 8 and half hours flight kusan in total silence muka yi shi, na lira daddy ya ssmu bacci sosai dan daga alama rabon da yayi bacci tun san da aka kwantar da ni, ni kuma a nawa bangaren kokawa muka ringa yi ni da baccin, shi yana so ya dauke ni ni kuma ina iyakacin kokarin ganin cewa bai dauke ni din ba, I needed to stay awake and alert dan in samu damar planning on my revenge on Gidado da Safina. Ban samu bacci ba sai bayan da muka sauka a lagos muka sake shiga wani jirgin zuwa. Ban samu bacci ba sai bayan da muka sauka a lagos muka sake shiga wani jirgin zuwa Abuja after waiting for 30minutes. Tun a Lagos din naji Daddy yana ta waya da Mustapha da kuma Mommy yana basu labarin abinda ya faru, ya kuma gaya musu gamu nan zuwa, sannan ya umarci Mustapha yaje airport a Abuja ya dauke mu sannan ya sanar da doctor din sa gamu nan zuwa dan zai sake dubani in mun karaso. Na fahimci su Mommy har lokacin a cikin hidimar biki suke, a lokacin ne kuma na tuna da cewa yau ne da daddare za'a yi dinner, a yau din ne kuma za'a kai amarya, dan haka na fara planning din yadda zan hargitsa dinner din sannan in tabbatar da cewa first night din su is the worst in history of marriages. Karfe biyu na rana da yan mintuna muka isa Abuja, da kyar na iya mikewa daga kan kujerar da nake kai saboda yadda gabaki daya jikina yake min ciwo sannan gurin aikina yana ta yi min zugi. Duk da ma na kwantar da kujera ta ba wai a zaune nake sosai ba. Ban iya tashi ba sai da wata maaikaciyar jirgin tazo ta kama ni muka tafi a hankali. Muna fita waje na hango Mommy da Mustapha, Mommy ta taho da sauri inda nake tana kare min kallo sannan ta juya gurin Daddy shima ta bishi da kallo "me ya same ku?" Ta tambayi no one in particular, babu wanda ya amsa mata sai ta karbe ni daga hannun air hostess din ta cigaba da tafiya da ni zuwa motar da suka zo da ita. Mustapha kuma ya cigaba da tura. Mustapha kuma ya cigaba da tura wheelchair din Daddy. Muka karasa motar ya taimaka masa ya zauna a gaba sannan ya saka wheelchair din a boot din motar ya shiga gaba mu kuma muka shiga baya ni da Mommy. Na jingina kaina a kujerar motar ina kallon titi da motoci da tituna da gidajen da muke wucewa. A zuciyata nace Nigeria my dear country, na dawo, let's see what you have in store for me a wannan karon. Na lura da ga Mommy har Mustapha kwalliya ce a jikin su, kwalliyar bikin Safina. Tun da muka shiga motar Mommy bakin ta bai yi shiru ba tana ta fadan me yasa muka taho a cikin halin rashin lafiya. Tace kuma laifi na ne tunda a waya Daddy yace mata ni ce na takura sai na dawo gida "kin san cewa duk abinda kika fada kamar yankan wuka ne a gurin sa, in baki damu da taki lafiyar ba ai ya kamata ace kin damu da tasa". Ni dai ban amsa mata ba, da ta cigaba ma sai na saka hannayena biyu na toshe kunnuwana sannan na rufe ido na. Can ness na jita tace "shikenan ai" sai kuma tayi shiru. Asibiti muka fara zuwa, muna zuwa suka fara daukan vitals din mu a take suka sake admitting Daddy. Ni kuma suka rubuta min bedrest har sai sunce otherwise. A can twins suka zo suka same mu. Suma daga gani daga gurin bikin suke. Suka rungume ni da murnar gani na. Ina jin Daddy yana musu magana "careful, bata da lafiya" suka cika ni suna kare kin kallo sannan Hassan yace "you look terrible" nayi kokarin yi masa. "you look terrible" nayi kokarin yi masa murmushi amma na kasa. Mommy suka fita da Mustapha zata tura shi airport ya dauko wasu kawayen ta da suka zo dinner din da za'a vi yau. Suka barmu ni da Daddy da twins. Daddy yace musu su dauke ni su tafi da ni gidan mu na nan garin "ba gidan bikin zaku kai ta ba. Ba kuma gidan Ahmad ba. Ku kaita gida ta huta, and stay with her" suka gyada kai a tare. Har na mike zan tafi sai ya kira sunana, "zo nan" daga yadda yayi maganar nasan fada zaiyi min amma sai naji ban san laifin da nayi ba kuma. Su Hassan suka fita ni kuma na zauna a kujerar da take kusa da gadon da yake ya sunkuyar da kaina kasa sai ace "Safiyya. Baki gaishe da Sa'adatu da Mustapha ba why?" Nayi shiru ina jujuya hannuna yace "har yanzu fushi kike yi dan sun taho sun bar mu?" Still ban ce komai ba. 21 11 1 7:46 PM Ya sake kiran sunana "Safiyya" na amsa a hankali, yace "Make peace with Sa'adatu and her children. Kinji ni?" Na gyada kai na kawai. Amsa ta bata gamsar da shi ba sai ya sake cewa "kiyi min alkawarin ba zaki yi rigima da su ba" na dago kaina ina kallon sa, he looked so sick and tired, shine mutumin da yafi sona fiye da kowa a duniya, shine mutumin da nafi so fiye da kowa a duniya. Nace "nayi alkawari Daddy. Ba zanyi rigima da su ba" yace "good" na sake mikewa yace "and one more thing" na sake dawowa na zauna vace "wave Muhammad?" zauna yace "waye Muhammad?" Nayi sauri na kalle shi da mamaki. Lokaci daya mood dina ya chanza daga indifferent zuwa tashin hankali. Yayi ajjiyar zuciya yace "so, shine baban Adam kenan" na fara girgiza kai na "Daddy.…... Muham.…waye Muhammad?" Yace "oh ni kike tambaya kenan. You call his name sau ba adadi sanda baki da lafiya. And now you are telling me baki san waye ba. Gashi kuma fuskar ki ta nuna alamar rashin gaskiya karara. Na fahimci shine baban wancan yaron. Na fahimci kuma kina sonsa sosai shi yasa kike cigaba da boye min shi dan kar inyi punishing dinsa for what he did. Just tell me who he is. I am not going to do anything to him a yanzu. I just want to give him his son. I just want that innocent baby to have a father" Na fara hawaye "Daddy ba nashi ba ne ba" babu abinda yake tayar min da hankali a duniya irin kin yarda da ni da Daddy yayi. Yayi shiru bai sake cewa komai ba har Mommy ta dawo. Na goge fuskata da sauri amma sai da ta lura da hawayen tace "har yanzu ana nan ana fama kenan" na kalli Daddy sannan na gaishe ta. Ta amsa shortly. Ina zama a mota na cigaba da kuka na. Hussein yace "yaushe zaki daina kuka ne wai yaya?" Ban amsa masa ba dan ni ma ban sani ba. Na dauka xasu tambaye ni ina baby amma sai naji duk basu tambaya ba, and I felt bad for little Adam. No body. and I felt bad for little Adam. No body wanted him. Not even his uncles. Gab da magrib muka shiga gidan. Esther ta tarye ni ta gaya min cewa dama Mommy tace ta gyara min dakina. Na shiga dakin na zauna twins suka shigo min da jakar kayana da Aunty Hajjo ta hado min da ga can. A ciki naga handbag dina, a cikin ta kuma naga wayata da na yar a dakina a Berlin san da na ga hoton Muhammad da Safina. Already wayar har ta mutu charji ya kare. Ina zaune Hassan ya dawo da tea a hannunsa ya hado min, Hussein kuma yaxo yace "yaya ko in hada miki smoothie irin wanda kike sha kullum?" Na girgiza kaina kawai ina jin babu dad yadda suke ta kokarin kyautata min amma na kasa ko da yi musu magana ne. Na bude jakar tawa na dauko wani dan karamin hoto na rike a hannuna ina kallon sa. Hoton mace da yayan ta mata guda uku. Na shafa fuskar wacce take mahaifiyata a cikin su ukun. She suffered more than suffering din da nake ciki, She lost more than abinda ni na rasa a yanzu, She almost lost me too, but then she gave her life for mine, Amma duk da yadda rayuwar tata ta kasance, she never lost hope, She kept her head high and she achieved fiye da yadda tunanin mai tunani zai tunano masa, Na ajiye hoton. And so will 1 Na dago kai ina kallon Hassan da ya saka ni a gaba yana kallo kamar zai yi kuka nace. a gaba yana kallo kamar zai yi kuka nace *karfe nawa ne dinner din Safina?" Yayi mamakin tambaya ta amma sai ya kalli agogo yace "7pm dai suka saka a kati. Though sunce babu African time dan a yau za"a kai amare bayan dinner din" na tambaya "amare?" Yace "eh, su biyu ne ai, akwai sister din mijin yaya Safina, tare aka hada auren nasu" "Mufida" na fada a hankali, yace "kin san ta ne?" Ban ce komai ba sai na dafa gado na mike. Shima ya mike da sauri yana kokarin rike ni. Nace "Okay. Let's get ready kar mu makara" ya bude ido "kar mu makara zuwa ina? Mu mun fasa zuwa ai tunda Daddy yace mu zauna da ke. Ke ma baki fa da lafiya ba zaki iya zuwa ba" na kirkiro murmushi nace "dan inje dinner din nan na taho tun daga Germany da sabon yanka a cikina, bana jin akwaí abinda zai hana ni zuwa", 17 11 7:46 PM Na shiga toilet na tsaya ina kallon kaina a madubi, saí a lokacín na kara fahimtar abinda twins suke nufi da suka ce I looked terrible dan da gaske I really looked terrible. Idona ya kara fadawa kasa ya kuma loosing all the light da suke cikin sa, fatar idon ta yamushe tayi baki, fatar lips dina ta bushe har tana neman tsagewa, ba zan iya tuna rabon da in shafa mai a bakina ba, ko a sauran jikina, Na tuna da da a gurina babban abu mai muhimmanci shine skin care routine dina, bana taba yadda inyi missing. Amma yanzu da rayuwa ta nuna min shege banga na fahimci komai ma guri yake samu. na fahimci komai ma guri yake samu. Sanitary pad din jikina na chanja na sake gyara kaina sannan na fito nace musu "na shirya, ku zo mu tafi" suka kalli juna sannan suka kalle ni, Hussein yace "yaya dinner ce fa. Kuma dangin angon nan naga manyan mutane ne sosai. It is going to be extravagant ....." Na yafa mayafi na nace "ba zuwa zanyi dan in burge kowa ba, zuwa zanyi dan inyi wa yar uwata murnar sabon auren ta. Wanda yaga ni ko shigata basu yi masa ba sai dai ya rufe idon sa". Doguwar riga ce a jikina ta yadi. Rigar aunty Hajjo ce ta bani na saka da zamu taho saboda tana da girma sosai kuma yadin yana da laushi ba zai ke min famin ciwo na ba. Rigar duk ta chukwuikuye saboda zaman jirgi. Dankwalin rigar na daura a kaina na rufe dankararren gashina da na manta rabon da in taje shi. Sai kuma wani mayafi da ko kadan bai shiga da yadin ba dana dora a kafada ta. Ganin basu da niyyar tashi mu tafi sai na wuce su na ce "in kun gama ku same ni a waje", A parlor na zauna ina jiran su, Esther ta zo da sauri ta kunna min tv da ac, ni duk basu dame ni ba, so nake inyi sauri inje in aiwatar da abinda yake raina, Wajen 7:30 suka fito, still da alamar basa son inje, na mike tsaye "kun gama?" Suma basu chanja kayan jikin su ba, Hussain ya sake kokarin hanani fita "yaya bedrest fa aka baki" ban amsa ba nayi hanyar waje, sai kuma na dawo. amsa ba nayi hanyar waje, sai kuma na dawo da baya nace musu "a ina ne gurin? Akwai gatepass a hannun ku? Na iya mota ai zan iya kai kaina in ba zaku kaini ba". A dole suka fito muka shiga mota muka tafi, sai da muka yi nisa nace musu "kar ku gaya wa Daddy naje" basu ce komai ba. Muna zuwa mukayi packing a inda aka tanada, na zauna a mota ina kallon mutane suna ta shiga gurin, ga kida har ya fara tashi. Sai na rufe ido na ina kokarin karfafa zuciyata. Yau zan ganshi. Amma a matsayin mijin wata. A matsayin mijin Safina. Yayin da ni kuma nake matsayin matar wani. Matar Mukhtar. Sai da naga alamar gurin ya cika sosai sannan nayi karfin halin fita daga motar, tunda na fita naji alamar jiri yana neman dibana amma na daure dan bana son twins su sani, na taka a hankali naje har bakin kofar na bayar da katin da twins suka bani sannan na shiga. A gurin muka rabu da su su suka tafi bangaren maza ni nayi na mata. Dama abinda nake so kenan. Ina kallon security din yana bina da kallo, maybe ya dauka almajira ce, Daga can karshe na samu guri na zauna saboda bana son wanda ya sanni ya ganni, Duk da dai nasan a yadda nake din nan ba kowa ne wanda ya sanni zai gane ni ba, A haka har guri ya gama cika aka fara gabatar da event, Ina ji aka yi announcing zuwan iyayen su Muhammad da Mufida, suka shigo cikin isa da burgewa. Sannan aka shigo da iyayen angon Mufida, suma suka wuce, sal iyayen amaryar. suma suka wuce, sal iyayen amaryar Muhammad, wato Safina, Mommy ce a gaba da yan uwanta suna take mata baya, nayi ajjiyar zuciya, wato ta baro mijin nata a asibiti ta taho dinner. Daga nan kuma sai aka y announcing shigowar angwaye da amare. Na mike tsaye daga inda nake ina hango kofar da zasu shigo ta cikin ta. Su Muhammad ne a gaba. Ido na fuskarsa ta fara gani. Yayi kyau iyakacin yadda dan Adam ya kamata yayi kyau. Gefensa ga yayata nan Safina, taci kwalliya ta ajin karshe, fuskar ta dauke da murmushi idonta a kasa kamar mai jin kunyar mutanen gurin. A bayan su abokan Muhammad ne, most of which na sansu, da kuma kawayen Safina, gabadayan su na san su. Kowannen su cikin kwalliya ta alfarma kuma cikin farin ciki. A raina nace gabakidayan su munafukai ne, tun daga kan Muhammad din har zuwa kan securities din gurin, duk munafukai ne. 25 14 7:46 PM Sai naji a raina ina fatan ina ma dai ginin gurin ya rushe ya fado a kan mu gabaki dayan mu mu mutu kowa ya huta. Ina na tsaye har suka je suka tsaya a tsakiyar fage, aka ringa kiran iyaye suna yi musu ruwan kudi, daga inda nake ina hango yadda Mommy take watsi da kudi. Kudin da ba ita ta nema ba, Sai da aka gama aka ce suke su zauna. And those minutes daga shigowar su zuwa zaman su, zan iya cewa are one of the most terrifying minutes of my. are one of the most terrifying minutes of my life. Suna zama aka yi announcing shigowar Mufida da angon ta. Nan da nan sai hankalin mutane ya koma kansu. I took my chance. Burina shine in hargitsa bikin ba tare da nayi calling attention din mutane zuwa kaina ba, not that I care about mutane, but bana son Daddy ya sani. Bana son yasan komai. Na bi ta gefen mutane har sai da na wuce inda mutane suke zazzaune. Ina jin jiri yana dibana amma na cigaba da daurewa. Daga inda nake ina hango Muhammad da Safina akan kujerun da aka tanada saboda su. Idonsa yana kasa yana daddanna wayarsa, ita kuma tana magana da wata kawarta Husna. Na taka a hankali na tafi inda suke idanuna a kansa, zuciya ta tana jera duk irin zagin da ta iya tana yi masa. "Munafiki. Mayaudari. Maci amana" sai dai kuma kiran tasa zuciyar take yi, so take ya amsa, so take ya dago ya kalli cikin idona ya gaya min dalilin da yasa ya auri yar'uwata. Tamkar wanda tasa zuciyar taji kiran tawa, sai ya dago idonsa a lokaci daya suka fada cikin nawa. Ina kallon sanda wayarsa ta zame daga cikin yatsun hannun sa ta fadi akan carpet din gurin. Ya mike tsaye a hankali kamar wanda ake jansa da zare. Na cigaba da tafiya idona a cikin nasa har sai da naje na tsaya a gabansa tsakanin mu bai fi taku daya ba. taku daya ba. Sai a lokacin Safina ta ganni, ta zabura kamar wadda aka watsawa wuta. Na dauke ido na daga cikin nashi na mayar kanta nace "hello dear sister. Na taho daga Germany nazo nan gurin musamman dan ke, dan inyi miki HML. Happy Married life to you" na mayar da ido na kansa, har lokacin ni yake kallo da idon da ban san yadda zan kwatanta shi ba. Nace "and Happy married life to you too". Sai na juya a hankali na sauka daga kan stage din, doing everything in my power dan ganin na hana kaina faduwa a gurin, bana son Daddy ya sani. Wata kofa na gani a kusa da stage din, kamar masu rabon abinci ne suke fitowa daga ciki. Nayi sauri na shiga, na wuce su suna ta hidimar su, na ga wata kofa na sake shiga sai na ganni a waje, kamar filin bayan gurin ne. Na tsaya ina tsakar numfashi da sauri dan in samu in daidaita bugun zuciya ta, Ji nayi an finciko ni da karfi an juyo dani, saura kadan in karasa shidewa, Muhammad na gani a tsaye a gaba na fuskarsa da yana yin da ban taba ganin ta cikin sa ba, yanayin da ba zan iya kwatantawa ba, EPISODE EIGHTEEN 15 > 5 3 owner 2 7:43 PM Safiyya Episode Eighteen: New Couples Paid advert *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad.* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*, *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332*, Sai da nayi amfani da dukkanin karfin halin da rage a gare ni sannan na iya cire idona daga cikin nasa na sauke su akan hannu na daya rike sannan na sake kallon sa nace "careful, ni matar aure ce" ya kalli hannun, daga alama shi kansa bai san ya rike ba, sannan ya sake shi da sauri yace cikin daga murya "then what are you doing here? Me kika zo yi nan?" Nace "kamar yadda na fada muku a ciki kai da matar ka, zuwa nayi in taya ku murnar auren ku, ko kaga nayi wani abun ne bayan haka?" Ya fara girgiza kansa "no. no. no, nasan me kika zo yi gurin nan. Na san me ya kawo ki. You came here to torment me. Why me? Me nayi miki? Shin soyayya ta koma laifi ne ni ban sani ba? After all the yaudara ta da kika yi for years before kika ce min kina da aure and you asked me not to contact you again and you were pregnant and ......." "Ya kare min kallo "where the hell is your pregnancy?" Ya fada looking as confused as ever. Nace "wrong question. You asked the wrong question, Babu hadin ka da cikina and you have no right to asked for it. Now I will ask you the right question, Shin saboda kana tunanin na yaudare ka...." "Tunani?" Ya tambaya "kina magana kamar baki yi ba. Kin. tambaya "kina magana kamar baki yi ba. Kin yaudare ni kema kin sani, kin......" Na katse shi "is that why you marry my sister? Saboda kana tunanin na yaudare ka or do you really love her?" Nayi masa tambayar da ita ce take keeping dina awake all these hours. Ya tsaya yana kallo na kamar a lokacin ya lura da ni a gurin. Ya bude bakin sa a hankali "your.... ." Sai kuma ya juya ya kalli hall din da muka fito daga cikin sa "your sister?" Ya tambaye ni kamar wanda bai ji abinda nace ba sosai. "She is your sister" ya fada as a statement, not as a question "she is your Safina" ya sake fada a hankali, more like talking to himself. And in that moment I realized the truth. Bai sani ba. Bai san wa ya aura ba. And ni kaina ba zan iya cewa ga abinda naji a zuciyata a game da hakan ba. Yes I felt a relief, relief that he didn't intentionally do it. And then a surge of pity, pity for him. Wani tausayinsa naji ya lullube ni. He is innocent, his innocence yana daga cikin dalilan da yasa nayi deciding rabuwa da shi so that he can continue to live his innocence life. And now he got dragged back into it and tangled in a web da ni bansan yadda zanyi in warware shi and set him free ba. Na fara girgiza kaina a hankali ina ja da baya, sannan kuma na fara sauri zuwa bakin titi nayi sa'ar taxi ta sauke wata na shige ciki. Na rufe ido na ina mayar da numfashi ciki. Na rufe ido na ina mayar da numfashi na a hankali hannuna a dage da ciki na gurin da akayi min aiki dan ba jaramin azabar ciwo yake yi min ba saboda tafiyar da nayi da sauri. Sai da mai motar ya tambaye ni sau biyu sannan na samu na bude baki na gaya masa address din inda zai kaini. A hanya sai na samu kaina da kasa zabar tunanin da zanyi. Tun sanda na ga hoton Muhammad da Safina babu irin lissafin da banyi ba na abinda zanyi musu, a cikin jirgi kuma babu irin plan din da ban shirya ba na yadda zan hargitsa dinner din su. A cikin plans din nawa har da petrol nace zan siyo gallon daya in zazzaga a hall din in kunna wuta. But I didn't do any of my plans. But still I feel satisfied. My mission has been accomplished. Dan a yadda na bar Muhammad nasan dinner din nan ta kare a gurin sa shi da Safina. Shi da kansa zai hargitsa bikin nasu da kansa. Da kyar na iya shiga gida bayan an sauke ni saboda azabar ciwo, ina zuwa na samu na sha magani na kwanta a parlor, har wani gumi ne yake karyomin saboda azaba, a haka bacci ya dauke ni. Cikin baccin naji hayaniya, na farka amma ban bude ido na ba sai naji muryar Mommy tana masifa, 13 7 2 1 7:51 PM "Wallahi ba'a isa ayi mana wannan wulakancin ba, chafdi, Basu san wace Sa'adatu ba. Ba'a haifi wanda ya isa yayi min. Sa'adatu ba. Ba'a haifi wanda ya isa yayi min wannan wulakancin in yi shiru in barshi ba". Naji Muryar kanwarta da muke cewa Aunty karama "dan Allah ki bar maganar nan Sa'adatu. Tunda mun dauko yarinyar mun taho ba shikenan ba, dole ai zasu bio mu har gida su bada hakuri in dai suna so a kai musu ita". Na bude idona a hankali na kare musu kallo, Mommy ce tayi kicin kicin, daga dukkan alamu tafi awa daya tana fada, sai kanwarta Hajiya karama da wata kawarta. Sai kuma Safina a can gefen su ta kwanta ta kifa kanta akan kujera, da kawarta Husna a zaune a gabanta. Na mayar da ido na na rufe. Suka cigaba da maganganun su, a cikin maganar na fahimci suna fada ne akan wai tunda Safina suka shiga da mijinta gurin dinner suka zauna, shikenan ya tashi yayi tafiyar sa ya barta ita kadai a zaune. Mufida tana zaune da mijinta ita kuma Safina tana zaune ita kadai. Anyi ta nemansa an rasa inda yayi, anyi ta kiran wayarsa a kashe. Ita ma Safina tace bata san inda yaje ba. Dan haka sai concentrating bikin aka yi akan Mufida, ita kuma Mommy ta gaji da ganin yarta tana zaune a high table kamar decoration ta dauko kayarta tana masifa mutane suna bata hakuri ta fito daga gurin dinner din. Mommy ta cigaba da fada "kuma wallahi banga wanda ya isa ya kai min ya gidan sa ba a yau, Idan kinga an kai yarinyar nan gidan sa sai yazo har cikin gidan nan ya bamu hakuri tukunna", bamu hakuri tukunna". A yadda aka tsara bikin nasu a yau za'a kai amare gidajen su, daga gurin dinner za'a wuce dasu, amma Mommy yanzu tace ba za'a kai Safina ba sai Muhammad yazo ya bada hakurin tafiya da yayi ya barta a stage kamar flowar decoration. Na tashi na zauna ina jin ciwon ya danyi min sauki sannan kuma hayaniyar su tana kokarin saka min ciwon kai. Na gaishe su suka amsa min babu yabo babu fallasa dan duk rayukan su a bace suke, muka gaisa da Husna ita ma tayi min sannu tace taji ance bani da lafiya. Na amsa mata da "da sauki ai sosai. The worst is over insha Allah. Na kusa inyi getting my life back insha Allah" Na mike nace da Mommy zan koma daki in kwanta ta gyada min kai kawai. Ina jin Hajiya karama tana tambayar ta "wanna yarinyar wanne ciwo take yi ne haka Sa'adatu? Kinga yadda ta koma kuwa?" Mommy ta tabe baki tace "ulcer ce ta sako ta a gaba, tayi mata mugun kamu har sai da ta kai ani mata aiki a hanji. Yara ne kayi ta fama dasu akan suci abinci ba zasu ci ba wai su dieting suke yi, wai su sunfi son su rame, gashi nan ai ta jawo wa kanta rama mai guarantee". Ni dai na wuce na shige dakina tun kafin a fara yi min fada akan laifin da ban aikata ba. One thing da nake respecting mommy akai shine ko yanuwanta da suke uwa daya uba daya ba ta gaya wa abinda ya same ni ba, kuma ba ta bari sun ganni da cikin ba, kuma ba ta bari sun ganni da cikin ba. Ina shiga dakin na shiga toilet nayi wanka na gyara jikina nayi shirin kwanciya bacci, ina jin yunwa but I did not feel like eating anything and did not care. Sai kawai na kashe fitila nayi kwanciya ta, somehow I was satisfied with tafiyar da Muhammad yayi ya bar Safina, my bad girl part wanted more than that but na san idan da akwai abinda yake so kuma yake respecting a duniya sune iyayensa, ba zai taba disrespecting dinsu a gaban mutane ba. And at least she gets to sleep alone in her room today, maimakon a dakin Muhammad kamar yadda ta saka rai. Ina nan kwance idona a rufe naji motsi an shigo dakin nawa, sannan aka kunna fitila. Na bude ido naga Safina a tsaye a bakin kofa, idonta da alamun tayi kuka. Na koma na kwanta na mayar da idona na rufe. Naji alamar ta zauna akan gadon sannan naji tace "Safiyya….... An samu misunderstanding. Na san kina gain kamar nayi miki laifi. Amma ina so in gaya miki cewa coincidence ne. Ni ban san wanda na aura shine tsohon saurayin ki ba. Tunda ni dai baki taba hada ni da shi ba ban taba ganin sa ba sunan sa kawai na sani. Suna kuma yakan.... .." Na bude ido na na mike zaune na zuba mata ido sai tayi shiru ta kasa cigaba da maganar, na nuna mata kofa nace "Safina, with all due respect, get out of my room, Ke karyar ki ko sallah ma bata yi, it is making me nauseous, dan Allah ki fita tun kafin karyar ki ta saka ni aman takaici" Ta yi shiru tana kallona. Na sake nuna kofa "out I said. In na cigaba da ganin ki ko jin muryar ki tabbas za'a fitar da gawar daya daga cikin mu daga cikin akin nan". Ta mike tsaye har takai bakin kofa kuma sai ta sake juyowa tana kallo na tace "it is obvious kin dauki maganar da zafi da yawa, kar ki manta amma na farko ke a yanzu matar aure ce. Na biyu ya gaya min ke kika yi breaking up with him. Yes, na san yana son ki har yanzu amma kar ki manta shi namiji ne, namiji yana iya son yaya ya dawo kuma yaso kanwa ko da uwarsu daya ubansu daya, ballantana mu da babu hadin jini. And a matsayi na na mace, making him fall in love with me is going to be the most easiest thing ever. Ina miki fatan alkhairi ke da naki mijin." Nayi murmushi nace "mun gode, now go and open your room ki shiga ki jira har sai yazo gida ya baku hakuri sai kije ki saka shi ya so ki din". Na koma na kwanta na rufe idona ina jin zuciya ta tana tafasa, da gaske idan Safina ta cigaba da tsaya wa a gurin nan ta kuma cigaba da kiran kanta matar Muhammad za'a iya rasa daya daga cikin mu. Addu'a nake a raina ta fita din, ba dan ina gudun abinda zanyi din ba sai dan ina tunanin. nake a raina ta tita din, ba dan ina gudun abinda zanyi din ba sai dan ina tunanin mahaifina daya ke kwance bashi da lafiya. Bata fita ba din kuwa sai ta cigaba da magana. "Haka ne, zan jira shi kamar yadda Mommy tace. Na san kuma zai zo, kamar yadda na san cewa zai so ni kuma zai manta da ke, musamman idan ya san abinda kika yi, abinda na tabbatar ba ki gaya masa ba, abinda na san kunyar gaya masa ne ya saka kika zabi rabuwa da shi" Na sake mikewa zaune da sauri, sai da naji ciwona ya amsa, sannan na bude abin da na rufa da shi na mike tsaye ina kallon ta "are you threatening me?" Ta ja da baya, daga alama taji tsoron irin zuciyar da nayi kuma bata son ta karasa gawar da ba tata ba. A lokacin aka bude kofar dakin aka shigo, duk muka juya muka kalli wanda ya shigo din, Mukhtar ne, kallo daya yayi yin ya juya gurin Safina "ke! Me kike yi a dakin ta kuma? Fita tun kafin in kai ki asibiti wallahi" ta juya da sauri ta fita dan ita ta san ba karamin aikin sa bane yayi decorating fuskarta da mari. Sai da ta fita sannan ya juyo yana kallona "Fiyya. I am so sorry" na koma na zauna a bakin gado hawaye ya fara wanke min fuska ta, ina jin shi ya rufe kofar dakin ya taho inda nake ya durkusa a gaba na yana kallon fuska ta "I am so sorry Safiyya, Bansan abinda yake faruwa ba kenan. Sai da naje dinner dazu na ganshi, Kuma ban san kin zo gari ba. No body told me kin zo gari I would have ba. No body told me kin zo gari I would have been here with you", Na rufe idona da hannayena kuka ya sake kwace min gabaki daya. Irin kukan da kake idan ka samu wani wanda yayi understanding situation din ka to some extent. Sai ya tashi ya zauna a bakin gadon tare da jawo ni jikinsa yana bubbuga baya na a hankali da sigar lallashi, "it is okay. Ki daina kuka kinji? I am here. Everything is going to be okay" and that was all I wanted, babban abinda nake bukata a lokacin shine wani ya rungume ni ya gaya min cewa everything is going to be okay. And that made me feel safe with him. He gave me heart warming words and a shoulder to cry on, and I did cried on his shoulders, ban san lokacin da na dauka ina kuka a jikin sa ba and in that few minutes I felt the safest I have felt in months. The next thing da ya dawo dani back to reality was the feeling of him trying to put his lips on mine. Trying to kiss me. Na bude ido da sauri ina kallon sa, ina jin safe heaven din da na ke tunanin na samu ta dawo tana crashing on me. Na saka hannu biyu na tura shi baya da karfi amma saboda girman sa da kuma rashin karfin jikina maimakon shi yayi baya sai nice nayi baya na tafi zan fado daga kan gadon, Ya tare ni da hannunsa daya dan kar in fadi, nature hannun nasa na mike tsaye jiri yana dibana "get out!" Na nuna masa kofa "fita. dibana *get out'" Na nuna masa kota "fita min daga daki* ya mike tsaye vana sake kokarin rike nì, "Safyyya! I am sorry! I was just trying to...." Ban cigaba da jin abinda zai ce ba na wuce shi na shige toilet tare da rufe kofa. 18 751 PM A cikin toilet din na kwanta a kasa a akan tiles, kukan nawa gaba daya ya dauke, tunani na ma gaba daya ya dauke. *Him Ranar daurin aure.... Kamar a mafarki haka yaga any daurin auren an gama, mutane suna ta mika masa hannu suna yi masa murna shima yana mika musu suna yin musabaha sannan sai mai hoto ya dauke su hoto, amma yaki barin zuciyarsa tayi processing abinda yake faruwa ballantana tayi accepting. Ba zai iya gane da wa da wa suka gaisa ba ba kuma ya gane mai suke cewa, he just smiled at people and answered Amen idan sunyi masa addu'a. Ya san kuma sun shiga gidan su Safina sunyi hotuna da ita sun kuma yi hotuna da mutane da yawa a gidan, Kamar kowa so yake yayi hoto da su, daga nan suka fito suka dauko hanyar gida, Sai da suka zo Abuja mutane suka fara raguwa sannan ya samu damar kasancewa shi da tunanin sa. Shi ya san shi ya zabi. auren nan a lokacin da aka bashi choice tsakanin yin auren ko barin sa, he thought tunda auren shine abinda ya fahimta a matsayin zabin Allah then it is going to bring him happiness. But me yasa instead of happiness yake jin wani feeling a zuciyarsa wanda ya kasa fassarawa? Ji yake kamar akwai wani bomb da yake ticking a cikin sa wanda yake gab da exploding ya kuma tarwatsa shi. Suna zuwa gida ya dauki uzuri yace baya jin dadi zai je ya kwanta. Kuma da gaske baya jin dadin, sai dai ya kasa tantancewa idan zazzabi yake yi ko ciwon kai ko ciwon zuciya? Dan haka kawai yasha maganin da Mama ta bashi ya kwanta ya rufe idonsa. Washegari assabar suka tashi da hidimar daurin auren Mufida, tun da assuba bai samu kansa ba yana ta kokarin yadda za'a sauki bakin Abba cikin girmamawar da suka yi deserving. Har ake je akayi daurin auren aka yi reception duk kusan shine akan komai, zuwa dare yayi gajiyar da a nasa daurin auren ma bai yi irin ta ba. Ranar Lahadi kuwa tunda yayi sallar asuba ya bar gidan ya koma gidan da yake zama a yanzu, yana saka ran zai kasance shi kadai tunda yan'uwan sa should be a gidan su gurin biki tunda biki da ma suka zo, amma bai jima da shiga gidan ba sai gasu sunzo mota mota, suka gaya masa ai ba gurin biki suka zo ba gurin sa suka zo, Haka suka saka shi a gaba da hirar aure, Yace "dan Allah ku rabu dani, na gaya muku bana jin dadi" AbdulShakur. na gaya muku bana jin dadi" AbdulShakur yace "baka jin dadi? Me yake damunka? Ko tsoron auren kake ji? Babu abin toro a ciki fa kawai da mun raka ka mun tafi sai ka lallabata ka bata kaza da lemo, shikenan sai ka saka ta a daki". Gidado ya bude ido yana kallon sa "kai fa dan iska ne" suka kyalkyale da dariya. Ayaan yace "wait, he is telling the truth ai, in baka saka ta a daki ba to a parlor zaka saka ta? In kuma baka san me zaka yi mata a dakin ba sai ka fada muyi maka bayani dalla dalla. Ga Al'ameen nan. He have been there. Ka zauna ka dauki darasi" Al'ameen ya gyara zama tare da gyaran murya "I am glad you guys realized girmana kuma kuka bani. Ni nake da experience ni zan bada wannan darasin". Gidado ya mike tsaye suka jawo shi suka sake zaunar dashi. "Ka zauna a gaban babban malami Sheikh Muhammad Al'ameen ka dauki darasi" ya ga dai ba rabuwa zasuyi da shi ba sai yace "to wai ku ya akayi kuka san cewa banfi shi Al'ameen din ilimin cikin bedroom din ba?" Al'ameen yace "kai yaro tsaya matsay in ka. Idan manya suna magana kayi shiru da bakin ka. Ka bari sai zuwa nan da kamar jibi sai in fara saka ka a ajin kusa da nawa". Gidado yace "ka daina cika baki fa, shi wani ilimin ai ba sai an shiga aji ake daukan karatu a kansa ba", A haka suka shashance har azahar, daga nan kuma suka fita suna karasa last minute preparations dinsu na dinner kowa yana so. preparations dinsu na dinner kowa yana so ya kure adaka dan a samu damar yin new catch ko kuma a burge current budurwar da ake da ita, a lokacin ne bayan sun kebe da Al'ameen yake gaya masa "ni fa bana son zuwa dinner din nan" Al'ameen ya bata rai "ai kuwa kasan baka isa ba. A ina ka taba ganin anyi dinner babu ango?" Gidado ya bata rai "kai kadai zaka gane halin da nake ciki tunda kai kadai kasan gaskiyar maganar nan, amma kuma kai ma ba zaka gane ba" Al'ameen yace "to ka ganar da ni mana?" Gidado yace "bana jin dadi. 21 4 3 7:51 PM Amma ba zaka gane me yake damuna ba, nima kaina ban san me yake damuna ba" sai Al'ameen ya yi shiru kawai ya rabu da shi dan bashi da amsar da zai bashi. A motar Al'ameen suka je suka dauki amarya, Al'ameen din ne yake tukawa Avaan a gaba, Gidado kuma yana baya. Suna sane suka yi haka wai dan Gidado ya zauna shi da amaryar sa a baya, sannan kuma Al'ameen ya saka Ayaan a gaba dan kar wata a kawayen amarya tace zata shiga kusa da shi, "Kar tsautsayi ya sa Humaira ta gani yau in kwana a kofar dakin ta ina bata hakuri" Ayaan yay dariya "kar ka bada maza mana" Al'ameen ya girgiza kai "no.…. Babu wannan maganar kaji, Maganin kar ayi kar a fara", Sai da kawayen amaryar kuwa suka yi musu mitar basu bar gurin babbar kawar amarya ba, Sannan suka fito da amarva ta shiaa. ba. Sannan suka fito da amarya ta shiga kusa da angonta suka tafi sauran kawayen ta kuma duk suka shiga motocin da aka tanada saboda su. A hanyar ne Safina tace masa "kayi kyau sosai" ya dago kai daga danna wayar da yake yi kamar wanda ya manta a inda yake yace "ohh. Thank you. You too" ta gaishe da su Al'ameen, suka amsa mata da faraar su da tsokana, tace ta gane Al'ameen, amma bata gane Ayaan ba. "Ko kai ne Sahabi?" "Sahabi?" Suka maimaita a tare, "waye Sahabi?" Al'ameen ya tambaya, tace "abokin ku mana Sahabi, I wanted to know his friends and he mentioned Sahabi, har ranar nan cikin dare yace zai kira shi a waya, sai na fahimci they are very close" "Sahabi?" Al'ameen ya sake maimaita wa dan baya jin akwai wani very close friend din Gidado wanda bai sani ba, Gidado yayi sauri yace "Sahabi mana, Ya Amen Sahabin ka manta?" Al'ameen yace "ohh that Sahabi, ai yayi tafiya ne shi yasa, bai zo bikin ba". Bayan sunje gurin event din sun jima a mota kafin ayi musu magana su fito, already tun kafin su shiga shi Gidado har ya gaji. Suka fito aka gama jera su kamar zasu je assembly a makaranta sannan aka ce su shiga. He walk kamar har zuwa inda aka ce su tsaya and he stood, aka yi tayi musu liki from both his side and Safina's side, sannan aka ce suje su zauna, Suna zama ya dauko wayarsa ya fara dannawa ba tare da yasan me yake. dannawa ba tare da yasan me yake dannawar ba, just to get away from what was happening around him. And the he felt it..... That feeling da ya ke ji a duk lokacin da take kallon sa, that feeling da yake ji idan yana tare da ita, he looked up and he saw her, amma farkon abinda ya fara zuwa zuciyar sa shine hallucinations yake yi. Dalili na farko shine me zai kawo ta gurin? Dalili na biyu kuma shine sam bata yi fitting da gurin ba. Bata ma yi fitting da kanta ba. She looked like yan gudun hijirar da suka shigo cikin gari bayan spending weeks a cikin daji, sannan aka basu kwancen kaya, kayan da suka yi musu yawa. Shi a ganin sa ba ta yadda za'a yi Safiyya, Piyan sa, ta zama haka. Dan ita din first class ce a cikin yan gayun da ya sani a rayuwar sa. She came and stood in front of him, she talked to Safina and then to him amma shi duk bai ji abinda tace ba. Sannan ta sauka ta bi ta wata hanta ta fita daga gurin. Sai a lokacin hankalin sa ya dawo jikin sa, shin da gaske Safiyya ce tazo ta tsaya yanzu a gabansa ko kuma hallucinations yake yi? His only chance of knowing the answer shine ya bita ya gani idan da gaske ita din ce, and he followed kofar da ta bi da sauri ya wuce masu rabon abinci ya fita filin baya. He saw her again and they talked or rather argued, abinda ya tabbatar masa da cewa mutum ce da gaske kuma Safiyya ce. A lokacin ta gaya masa maganar da ta karasa tarwatsa. masa maganar da ta karasa tarwatsa tunanin sa, ta gaya masa cewa Safinar da ya aura tabbas ita ce Safina yayarta. She left him frozen a tsaye for a moment, and then yayi kokarin binta but was held back by Al'ameen da ya fito neman sa "lafiyar ka Muhammad, ina zaka je? Me kake yi anan?" Gidado ya juya yana kallon Safiyya da take kokarin shiga abin hawa "Safiyya ce. She was here. She was..." Ya juya ya kalli hall din "that bitch lied to me. Makaryaciya ce. I was right. I was right all along and she lied". 12 9 7:51 PM Muhammad Al'ameen ya tsaya yana kallon sa cikin rashin fahimta, Gidado ya juya da niyyar komawa ciki da sauri yana cewa "I will deal with her wallahi sai ta gane kuren ta. Sai ta san ni tayi wa karya" Al'ameen ya rike shi "lafiyar ka Muhammad? Maganar wa kake yi ne?" Ya juyo yana kallon shi idanunsa reflecting irin rage din da yake cikin zuciyarsa yace "Safina. Karya tayi min ashe, Ita ce yayar Safiyya, Wallahi sai na yi mata hauka yau" Muhammad Al'ameen ya rike shi ya hana shi shiga a daidai lokacin da Haidar shima ya fito gurin yana kallon su da alamar tambaya a fuskarsa, Al'ameen yace masa "Haidar, sauri, dauko min mota" sannan ya juya gurin Gidado yace "zakayi mata hauka amma ba'a nan ba, Ba zaka yi mata hauka a gaban iyayen mu da bakin su ba". ba" Daga haka ya saka shi a motar da Haidar ya dauko ya ja suka bar gurin. Gidado ya jingina kansa a jikin kujerar motar yayi shiru, yana jin Al'ameen yana ta magana amma baya fahimtar abinda yake cewa, ya san dai hakuri yake bashi da kokarin kwantar masa da hankali, ya dago kansa a hankali yana kallon hannun sa yace "her hand looks and feels like a stick, why?" Ya juya yana kallon Al'ameen da bai gane tambayar me yake yi masa ba, ya sake yi masa wata tambayar "she was pregnant and now she isn't". Anan Al'ameen ya fahimci maganar wa yake yi sai yace "Gidado, masu ciki suna haihuwa. Baka tunanin haihuwa tayi" Gidado ya girgiza kansa "ba haihuwa tayi ba, cikin bai isa haihuwa ba. I want to know what happened to her. I will find out what happened to her. And I know where I can get my answers from". Maman Maama 29 16 15. EPISODE NINETEEN owner 26 3 8:04 PM Nafisa Tafida Usman Safiyya owner Episode Nineteen: Baba Hadiza Paid advert *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad.* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*. *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332*. Her • Wani irin sanyin da yake ratsani ne ya tashe ni daga baccin da bansan sanda nayi shi ba, ban kuma san dadewar da nayi ina yin sa ba. Na bude ido na tare da kara takurewa a guri daya a lokacin da na fahimci cewa a toilet nake kwance akan tiles. Sanyi nake ji har cikin kashi na. Da kyar na iya mike wa saboda karkarwar da jiki na yake yi. Ina mikewar kuma sai naji gurin aikina ya fara wani irin zugin azaba kamar wanda dinkin ya ke budewa. Da kyar da daddafa bango na fito daga toilet din na koma daki a daidai lokacin da naji ana kiran assalatu. Wato dai a toilet din na kwana. Abubuwa ne da yawa suke faru wa da ni a lokaci daya, azababben sanyi nake ji har cikin kashi na, azababben ciwo nake ji a gurin da aka yanka cikina, ga kaina yana wani irin sarawa kamar zai sage gida biyu, ga wata irin yunwa da nake ji wadda ta tuna min da cewa rabona da abinci tun a Berlin da Aunty Hajjo ta bani. A carpet na sake kwanciya saboda karkarwar da jiki na yake yi ya hana ni karasawa kan gado, Na daga hannuna da kyar na jawo blanket din da yake kan gadon ya fado jikina. Na sake takurewa a guri daya ina karkarwa tare da ambaton sunan Allah, a raina kamar kullum ina fatan zai dauki raina a ranar in huta. Bakin cikin duniya dai ai mai. a ranar in huta. Bakin cikin duniya dai ai mai rai ne yake jin sa ko? In babu ran ba shikenan ba? Na fara lissafa wadanda zasu yi kewa ta idan na tafi. Daddy na ne na farko, duk da dai babu wanda ya san gawar fari amma ina saka ran cewa shima ba zai jima ba idan na mutu zai bini. Daga Daddy sai Muhammad, saw my love burning in his eyes jiya da daddare, daga dukkan alamu plan dina na cire soyayya ta daga cikin zuciyarsa idan nayi breaking heart dinsa did not work, and I pity him for that, but na san babu abinda time baya healing, he will get over me a hankali musamman idan ya tabbatar da cewa bana duniya. The last one is Junior, he will grow up maraya, fatherless, motherless, without even a single grandfather, or a single relative dan na san a dangina babu mai daukan sa ya kira shi da jinin sa, except idan bayan mutuwa ta Daddy did to him abinda Ammi tayi min, idan kuma hakan ya faru da shi to kuwa tabbas sai nafi tausaya masa akan kasancewar sa maraya. Because the vultures will turn to feed on him a hankali a hankali har sai sun rabashi da komai kamar yadda suka yi min, Kamar yadda suka raba ni da komai da yake da value a rayuwata and then discard me to die in the toilet, Na tuna da gata na, da ace da ne babu yadda za'a yi in kwana a cikin toilet kuma wai babu wanda ya sani because no one cared to look for me duk kuwa da cewa. cared to look for me duk kuwa da cewa gidan a cike yake da mutanen da suke kiran kansu da yanuwana. Bunch of munafukai. Duk kan su munafukai ne. And every single one of them played a role in kasancewa ta a halin da nake ciki a yanzu. Mukhtar included. I chose to marry Mukhtar saboda bani da wani zabi kamar yadda na gayawa Daddy na. Dalilin zaban sa akan sauran kuma shine kasancewar Mukhtar ya jima yana sona. Ya furta cewa yana son aure na tun kafin yasan gaskiyar wacece ni. Wannan ya banbanta soyayyar sa da ta Mustapha and his mother. Duk da cewa deep down na san cewa soyayyar tasa ba ta gaskiya ba ce ba but at least he did love me in his own way. Amma a daren jiya ya tabbatar min da tasa kalar soyayyar, ya tabbatar min da abinda nake tunani a cikin zuciyata. A ganina babu wanda zai min soyayya ta gaskiya sannan ya tarar da ni a halin da ya tarar dani jiya sannan har ya nemi wani abu a guri na. Wani abu a jiki na. At least na tabbatar Gidado ba zai taba min hakan ba. 24 16 3 A 1 8:15 PM For all the years that we have been together I have seen his desires of me in his eyes more times than I can count but he never ask me for it. Ko a waya kuma, He never even try kissing me duk kuwa da irin wayewar sa da kuma irin yadda rayuwa ta zama. Abinda yayi ta tambaya kuma yayi ta. zama. Abinda yayi ta tambaya kuma yayi ta naci akai shine aure. Abinda ni kuma naki bashi hadin kai akai. For all these months da nake cikin wannan tashin hankalin na san cewa daga cikin abinda ya saka Daddy yake daga min kafa mai kakkarya ni ba kamar yadda Mommy ta kan fada a lokuta da dama shine deep down him ya san cewa akwai laifinsa akan abinda ya same ni, sai dai bai taba furta hakan ba, nima kuma na san akwai laifinsa akan abinda ya same ni, amma ni ma ban taba furta hakan ba, and for all the parts da yake nashi ne a cikin maganar, na yafe mishi. And na yafe wa Ammi ita ma, for she thought she was doing the right thing for me. And now as I lay on the floor waiting and wishing for the hundredth time that malakul maut will visit me and end my suffering, I rewind my life back Idan nace my life, sai inga cewa bata bada ma'ana ba, dan ni din product ce of many things, dole rayuwata ba zata tsaya tayi zaman kanta ba sai na jingina ta da wadanda suka samar dani, mahaifiyata da mahaifina, saboda choices din su, losses din su and sacrifices dinsu sune suka y making and shaping rayuwata zuwa abinda take a yanzu, Asalin mahafiyata kamar yadda na samu labari daga Daddy, Mommy da kuma Hajiya. labari daga Daddy, Mommy da kuma Hajiya sun gaya min cewa yar garin Kura ce ta jihar Zamfara anan Nigeria. Anan tushen mahaifin ta yake, har yau kuma yanuwanta suna can amma kuma Daddy ya haramtamin zuwa gurin su, yace min kuma shima wannan wasiyya ce daga Ammi na, daya daga cikin many wasiyyun da ta bar min. A labarin nata na fahimci cewa mahaifiyar ta, ba yar Kura ba ce ba, yar wani kauye ne kusa da Kurar da ake kira kwatarkwashi, kauyen da ya samu sunan sa daga katon dutsen da yake kusa da shi, dutsen da ake kira dutsen kwatarkwashi. Sunan mahaifiyar tata Hadiza. Wadda Ammi take kira da Baba Hadiza. Hajiya tace babu wanda zai zauna da Safiya na awa daya bai samu kason sa a labarin Baba Hadiza ba. Kowa da ya san ta yasan cewa tana matukar son Baba Hadiza. Mahaifan Baba Hadiza Fulani ne makiyaya masu yawo daga wanna dajin zuwa wancan dan ciyar da shanun su, sun haifi yaya da yawa, Baba Hadiza ita ce yar autar su kuma sun haife ta ne a lokacin da girma ya riga ya zo musu har sun dauka sun gama haihuwa. Tun tana yar karama ne suka daina yawon kiwo saboda shekarun su da suka ja, suka bar wa manyan yayan su suka cigaba da yin kiwo su kuma suka zauna anan garin kwatarkwashi da niyyar karasa abinda ya rage musu a rayuwa. Anan Hadiza ta girma, Bata yi makaranta ba, Ta kan dai yi tallar nono da fura, da daddare kuma taje nono da fura, da daddare kuma taje makarantar allo inda ta koyi addini dai dai yadda zata yi sallah ta kuma zauna da mutane la fiya. A tallar noon ne ta had da Alhaji Haladu wanda babban mutum ne shi mai rike da mukamin mai unguwa a garin Kura. Haduwar ta su ta kasance sakamakon kadeta da yayi a babur din sa lokacin da yake sauri zai koma garinsa ita kuma tana sauri zata koma gida gudun kar duhun dare ya ritsa da ita a daji. Daga nan ya dauketa ya kaita chemist aka duba buguwar da tayi ya kuma kaita gidan su ya dankata a hannun iyayenta sannan ya yi musu nasihar su daina tura ta talla a matsayin ta na karamar budurwa saboda gudun kar ta hadu da bata gari a hanya. Anan ne suka nuna masa cewa babu ce ta saka su tura ta tallar, mahaifiyar ta tayi girma ba zata iya yin tallar ba, mahaifin yayi tsufa ba zai iya noma ba, sauran yara kowa ya kama gabansa, ita din dai ita zata tatsi nonan shanun da suka rage a gurin su taje ta siyar tayo musu awo ta kawo musu su ci abinci. Fahimtar hakan sai ya saka ya tausaya musu, daga nan sai kuma yayi alkawarin zai cigaba da daukan nauyin su sannan kuma ya nemi bukatar su aura masa ita. Daga farko sun ki yarda, musamman saboda yawn shekarun sa da kuma kankantar nata shekarun. Dan daga ganin sa sun san kananan yayansa sune zasu yi sa'annin Hadiza. Watanni kadan bayan wanna sai Allah yayi wa mahaifiyar Hadiza cikawa bayan yar karamar jinyar da Alhaji Haladu ne ya dauki nauyin siyan magani da komai, bayan ta rasu ma shi ya tsaya akai mata duk kan abinda addini ya tanada a ka kaita gidan ta na gaskiya. Wannan ya sa mahaifin Hadiza ya ga babu wani sauran gatan da ya rage zaiyi mata wanda ya wuce ya aurar da ita, kuma wa yafi dacewa ya aura wa ita wanda yafi attajirin da yake kula da su a yanzu? A haka aka daura auren Hadiza, baffan ta ya siyar da sauran saniya guda daya data rage masa a gabansa yayi mata kayan daki, sannan yanuwanta suka zo daga gidajen su aka hadu aka kawo ta gidan Alhaji Haladu dake garin Kura. Gidan babban gida ne irin gidajen attajiran kauye, katon tsakar gida da katuwar bishiya sai dakuna a hagu da dama, sai kuma babban zaure inda yake zama da mutanen sa, anan kuma kofar turakar sa take. Matan sa biyu kafin ya auri Baba Hadiza, Inna Gaje, ita ce uwargida, kusan duk yayanta sun yi aure sai autar ta sa'ar Hadiza, daga ita kuma sai Inna Sa'ade, ita kuma yaya maza Allah ya bata guda takwas, lokacin da akayi auren Hadiza guda uku daga ciki sunvi aure, bivu kananan suna. daga ciki sunyi aure, biyu kananan suna gabanta, ukun tsakiyar kuma duk sun tafi duniya neman kudi. Kusan ita ce mai kudin gidan dan yayanta abinda suke samu a kasuwa ya fi wanda shi kansa mahaifin nasu yake samu. Auren yar karamar yarinya Hadiza da Alhaji Haladu yayi ba karamin sosa ran matansa da yayansa yayi ba, musamman da suka duba suka ga tsantsar kyawun fuska da kuma kyawun surar da Allah yayi mata. A ganin su zata iya auren duk wani matashi mai jini a jika da take so, mai yasa ta auri mijin su? Amsar da suka bawa kansu shine son abin hannunsa ne ya kawo ta gidan. A bangaren Hadiza kuwa ita ba zata ce tana son Alhaji Haladu ba, ita ba zata ce tana son kowa ba ma saboda ita ba zata ce ta san menene so ba. Ita dai kawai ta san yana kyautata wa iyayen ta, daga nan kuma taji ance mata za'a aura mata shi, sai kuma aka aura mata shi din aka dauko ta aka kawo ta gidan sa aka watse aka barta daga ita sai shi sai mutanen gidan da suke: mata kallon hadarin kaji ba tare da tasan dalili ba. Da ace za'a bata zabi da zata so komawa dakin innar ta ta cigaba da kula da Inna da baffanta, ta cigaba da zuwa tallan nonon ta tana zuwa makarantar allon ta, Sai dai babu wanda ya tambaye ta zabin ta, babu wanda ya tuntube ta yaji ra'ayin ta, Hukunci kawai aka yanke mata aka kuma barta tare da consequences din hukuncin da ba ita ta yanke shi ba. consequences din hukuncin da ba ita ta yanke shi ba. Dakin Baba Hadiza shine a farko kana shigo tsakar gidan, katon daki ne sabon gini da Alhaji Haladu yayi musamman saboda amaryarsa. A ciki kuma aka zuba mata kayan dakin da baffan ta yayi mata, gadon karfe babba mai runfa da kuma gadon katako karami, sai dibaida a gefe da aka cika ta da samiru kanana da manya, tsakar dakin kuma an shimfida leda har bakin kofa, an kuma zagaye dakin gabaki dayan sa da labule. Kana gain dakin kaga dakin amaryar fulani yar gata. Sai dai ita Hadiza bata ji duk wanna gatan ba, tayi kewar iyayenta sosai musamman mahaifiyarta da ta san bata duniya. A hankali kuma sai ta fara sabawa, ta fara sabawa sosai da Alhaji Haladu dan yana matukar kyautata mata. Duk abinda take so shi zai yi mata wanda kuma bata so to shima baya son sa, baya barinta taci abincin gidan sai dai yaje ya siyo mata a waje, abinci mai dadi da nama, ya hado mata da kayan marmarin da ake yayi a lokacin, Gidan kuma kaf babu wanda ya isa yayi mata bakar magana, in ma zasuyi sai dai a bayan idonsa kuma yadda ba zai gane ba in yazo, dan ko chanjin fuska ya gani a gurin ta yayi ta tambaya kenan ko wani ne yayi mata wani abu, ko da kuwa bata kai karar kowa ba to sai yazo tsakar gida yayi ta masifa yana neman wanda ya taba masa amaryar sa. Ita. neman wanda ya taba masa amaryar sa. Ita a yarinyar ta sai ta kara daukan hakan a matsayin soyayya da gata. 11 2 8:15 PM Dan haka sanda mahaifinta ya rasu ma tayi kukan rabuwa da shi amma bata yi kewa sosai ba dan tana gain Alhaji Haladu ya maye mata gurbin uwa da uba. A haka Allah ya bata ciki, shima haka Alhaji Haladu ya sha rawar kafa, dan akwai sanda jama"ar gidan suka farka cikin dare suka ganshi a bakin murhu yana gasa masara, Hadiza ce tace tana son cin gasashshiyar masara cikin dare. Idan kuwa tayi amai, haka zasu ganshi a bakin rijiya yana wanke wa. A hankali a hankali duk matan suka fita sabgar sa, suka barshi shi da amaryar sa, yayan ma kuma haka, duk suka mayar da hankalinsu kan neman abin duniyar su. Haihuwa ta farko Allah ya bawa Hadiza diya mace, Alhaji Haladu ya tambaye ta sunan da take so a saka wa yar tata, ta kalli kyakkyawar jaririyar da take kan cinyarta mai kama da ita tace "Safiya. Na taba jin sunan a gurin wadansu yan birni da suka taba tsayawa a mota suka sayi nono a gurina, nima ina son idan yata ta girma ta zama yar gayu irin su, ita ma ta ringa tuka mota", A take Alhaji Haladu yay alkawarin idan yar ta girma zai siyar da babbar gonar sa ta bakin titi ya siya mata mota. titi ya siya mata mota. Safiya ta ga gata, duk wani kayan yan gayu da Hadiza ta gani zata ce a siya wa Safiya kuma Alhaji Haladu ko tasa sutturar zai siyar ya siya mata sai ya siya babu musu, har keken koyon tafiya ya tafi har cikin garin Gusau ya siyo wa Safiya Hadiza take dira ta akai tana tura ta a tsakar gida. Babu wanda yake tanka mata a matan gidan, ita ma kuma a yarintar ta bata damu da su kula ta ko a'a ba, ita dai zata gaishe da duk wacce ta san ta girme ta ko a matan gidan ko a yayan gidan, duk wadda bata amsa ba ma matsalar ta ce. Ta san dai babu mai taba ko da silin dogon gashin kanta ne. Shekaru biyu bayan haihuwar Safiya aka haifi Sauda. Shima sunan Hadiza ce ta zabe shi tace sunan wata yar garin su ne da take zuwa makarantar boko "har makarantar kwana take zuwa kuma ta iya turanci kamar baturiyar ingila" Alhaji Haladu yayi dariya tare da alkawarin ita ma wanna Saudan zata je makaranta "in ta gama makarantar kwanan ma har kasar waje zan kaita tayi wani karatun, sai ta hadu da turawan ingilan a can" daga nan kuwa Hadiza ta dage, ita lallai yar ta baturiya zata zama, A maimakon "war" ko "zo" da ta kan fadawa Safiya in zata kira ta, ita Sauda da "come" ta ke kiranta, bayan da ta matsawa Dada dan Inna Sa'ade ya koya mata "zo" da turanci, "Saboda in fara koya mata tun yanzu, yar boko zata zama, har ingila zata je tayl karatu", karatu". Sauda tana da shekaru uku aka haifi Khadijah. Ita kuma Alhaji Haladu ne ya zabi sunan yace "takwara zanyi miki. Amma sai bambanta ita ace mata Khadijah. Kuma dama gashi duk tafi sauran kama da ke". Hadiza ta kalli yarinyar tana jin dadi, ada bata san menene so ba, amma a yanzu ta san shi, ta kuma san cewa duk duniya babu abinda take so sama da yayanta guda uku. Kamar yadda Alhaji Haladu yake nuna wa Hadiza soyayya ido rufe haka yake nunawa yayanta. Alhaji har tsarki yake wa yaran idan sunyi kashi ko da kuwa uwar ba wani abin kirki take yi ba. Wani lokacin tana can tana shiriritar ta zai yiwa yaran wanka ya shirya su ya fita dasu zaure su zauna tare. Idan suna zaune kuwa duk mai abin siyarwar da tazo wucewa sai ya siya musu musamman idan ya fahimci suna so, kamar yadda indai aka kawo abin kwadayin da yasan Hadiza tana so sai ya siya mata ya aika mata dashi cikin gida ba tare da ya tuna da sauran matan sa ba. Idan sunyi korafi sai ya hau fada "yanzu wannan yar karamar yarinyar kuke kishi da ita? Yarinyar da kuka kusa yin jika da ita?" Ko kuma yace "marainiya ce bata da uwa bata da uba, Bata sana'a bata kuma da manyan yayan da zasu siya mata, Ku kuwa kudin da yake cikin zanin ku yafi na aljihuna yawa. Abinda yayan ku suke baku ko rabin sa basa bani ni", Tsinuwa, bakar magana, mugun baki, Tsinuwa, bakar magana, mugun baki, aibatawa, kyara, tsangwama babu abinda Hadiza da yayanta ba su gani ba a gurin iyalin Alhaji Haladu. Ita kuwa Hadiza babu abinda ya sha mata kai da su ko abinda suke yi. Ita a ganinta tunda dai ita bata yi musu laifin komai ba, abinda duk Alhaji yayi musu tsakanin su ne da shi. 15 4 8:15 PM Hadiza tana da shekaru ashirin da uku, Safiya tana da shekaru tara, Sauda bakwai, Khadijah kuma hudu. Alhaji Haladu ya kwanta bacci da daddare amma da safe bai tashi ba. Ya mutu a cikin baccin sa. Ya mutu yana da shekaru saba"in da hudu, ya bar yaya ashirin da matan aure uku. Mutuwar Alhaji Haladu ita ce dai dai junction din da Baba Hadiza ta fara girbar abinda ba ita ta shuka ba, ba ita ta zabi auren Alhaji Haladu ba, ba kuma ita ta kuma ta saka shi ya nuna mata soyayya ita da yayanta fiye da sauran matansa ba. In fact ita bata da hankali, wayewa da kuma ilimin da zata banbance dai dai da rashin dai dai, Iyayen ta da mijin ta su suka yi shuka, ita kuma ita da yayanta suka yi girbi. Maman Maama 4 36 24 3 2 EPISODE TWENTY 3 LTE 0 8:13 PM Safiyya Episode Twenty: The Tragic Family 1 Paid Advert *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad.* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*. *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332*, Tun kafin a binne Alhaji Haladu Baba Hadiza ta fara fuskantar cewa rayuwa ta chanja, dan da kyar, har sai da jama'ar unguwa suka saka baki sannan aka bar ta ita da yaran ta da basu ma fahimci me yake faruwa ba suka shiga gurin gawarsa suka yi bankwana da shi. Ta zauna a gaban gawar tana kallon sa, a zuciyarta tana yi masa addu'ar samun rahamar ubangiji, sannan kuma at the same time tana tambayar kanta yanzu yaya makomar rayuwar su kenan? Safiya wadda ita kadai ce a lokacin ta fara fahimtar menene mutuwa, ita ce ta zauna a kusa da Baba Hadiza ita ma tana kallon gawar Alhaji Haladu tana kuka, sai dai ita kukan sabo tare da alhinin rabuwa da babanta take yi ba wai na tunanin what's next ba. Saudat da Khadijah kam suma sunyi kuka, sai dai a nasu bangaren, ganin mahaifiyar su da yayarsu suna yin kuka ne ya saka su kukan ba wai dan sun fahimci abinda yake faruwa ba. Daga nan Malam Jamilu wanda su Safiya suke kira da yaya Malam saboda yana koyarwa a makarantar primary din su, babban dan Alhaji Haladu yazo ya kore su daga gaban gawar "kin ganshi ai, sai ki kwashi yayanki ku fita ku bamu guri mu shirya shi, kin wani saka shi a gaba kuna koke koke kamar kunfi kowa son sa" Hadiza ta mike jiki a sanyaye tana yiwa Alhajì Haladu kallon karshe, ganin tana cigaba da bata lokaci ne ya saka Jamilu ya damki. bata lokaci ne ya saka Jamilu ya damki kafadun Khadijah da na Sauda yayi waje da su, yaran suka sa ihu saboda zafin rikon da yayi musu, Hadiza tayi sauri ta biyo shi a baya "dan Allah ka sake su, dan Allah" ya ajiye su a tsakar gida ya juya yana cewa "yanzu ba gashi nan kin fito ba" ta jawo yaranta jikinta tana lallashin su, daga ita har Jamilu sun san cewa Alhaji Haladu da ya ke kwance a daki da ace da rai a jikinsa da ran kowa sai ya baci idan aka taba masa yan leken yayan nasa. Amma yanzu o da yana ji babu abinda zai iya yi akai. Akayi masa sutura aka yi masa Sallah kamar yadda addinin musulunci ya umarta sannan aka dauke shi zuwa gidan sa na karshe. Hadiza yayanta suka yi masa rakiya zuwa zauren gidan tare da sauran mata da yayan gidan, sannan suka tsaya suka kalla yayin da ake masa Sallah, suna kuma kallo aka dauke shi aka tafi dashi sannan suka dawo cikin gida knowing cewa ba zasu kara gain sa ba, Amma suna zama Khadijah ta jawo hannun Hadiza "Baba Hadiza, Baba Hadiza, wai ina Baba ya tafi ne? Ina aka kaishi?" Baba Hadiza ta jawo ta jikinta "ya tafi asibiti ne, bashi da lafiya shine aka kaishi asibiti gurin likita" Khadijah ta bata rai "ni so nake ya dawo ko kuma ke ki kaini gurin sa, zuwa zanyi in gaya masa yaya Malam (Jamilu) ya matse min hannu na". matse min hannu na". Kafin Baba Hadiza ta san amsar da zata bata sai Lami, daya daga cikin yayan Alhaji Haladu da take zaune a kusa da su tace "ba sai ki bishi lahirar ba ki gaya masa, kaji yarinya yar karama da shegen munafunci irin na gado? Da wannan munafunci ne dama aka raba mu da mahaifin mu, muna ji muna gani ya zamanto Baba baya jin maganar kowa a gidan nan sai ta su" Yar'uwata Balaraba ita ma ta karba "haba Lami, ke ma kinsan lamarin Baba da matar nan yafi karfin munafunci, kowa ma yasan asiri tayi masa [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: kowa ma yasan asiri tayi masa, surkulle ne kawai irin nasu a fulanin daji suka hada baki ita da iyayen ta suka yi masa suka raba shi da kowa suka wahalar da bawan Allah, yanzu dai wahalar sa ta kare Allah ya karbi abinsa, ita kuma gata nan ga gidan sai muga tsiyar da zata zauna a gidan ta cigaba da ci". Mutanen da suke gidan suka fara basu hakuri, "haba ku kuwa, daga tafiya kai shi ko binne shi ba'a yi ba? Ku yi hakuri ku bar maganar nan, shi sharri ai dan aike ne duk abinda tayi ma kanta zai dawo". 15 8 2 8:16 PM Hadiza ta fara share hawaye "wallahi babu abinda nayi masa, Allah ne shaida ta babu abinda nayi masa, iyayena ma kuma sun mutu kuma babu abinda suka yi masa" Lami ta mike ta tsaya akan Hadiza tana nuna ta da yatsa tace "to in kinyi masa ma Hadiza fada zaki vi? Mu ai duk mun san kinvi masan. zaki yi? Mu ai duk mun san kini masan kuma babu abinda zaki fada wanda zal saka mu yarda da ke, shi kuma ya riga ya mutu za kuma ku hadu a lahira ke da shi, munafuka algunguma... ." Safiya yar shekara tara ta mike ta saka dan karamin hannunta ta tura Lami baya "ki daina yi mata fada! Ki daina yi mata zagi! Ki rabu da ita!" Lami da abun yazo wa a bazata ta kaiwa Safiya duka, Hadiza tayi sauri ta tare sannan ta janye Safiya, bata kara yiwa kowa magana ba ta janye yayanta suka shiga dakin su suka turo kofa. Tana jiyo Lami tana masifa ana bata hakuri, ta kuma yi rantsuwar sai ta illata Safiya ko da ba yau ba. A haka Hadiza tayi going through zaman makokin nan, tana daki ita da yayanta sai dai makota da sauran abokan arziki idan suna son yi mata gaisuwa su bita daki. Ko toilet wata daga cikin yayan idan zata je sai Baba Hadiza ta raka ta saboda tsoron kar a taba mata yayan ta. Idan ta fita din kuwa kafin ta dawo sai an yar mata da magana. Tun daga lokacin suka fara fuskantar matsalar abinci, babu wanda yake zuba abinci a gidan yake basu, gashi kuma ita dama ba gwanar ajjiyar kudi bace ba ta saba duk abinda take so Alhaji zata tambaya shi kuma ya siyo ya kawo mata, babu kudi sam a dakinta sai bankin Safiya da take tara kudin tarar ta a ciki, in an bata bata kashewa sai ta saka a ciki. Da yunwa ta ishe su shi suka fasa Hadiza ta leka ta kira wani yaro. suka fasa Hadiza ta leka ta kira wani yaro dan makota ya siyo musu abinci a gidan su. To da yake matar suna mutunci da Hadiza sai ta dawo mata da kudin ta kuma tace take aikowa kullum ana karbar musu abinci kafin a share makoki. To da wannan abincin suka rayu a wannan lokacin. A ranar bakwan ne kuma yayan Hadiza Jabiru wanda a lokacin ya kado shanun sa zuwa garin yaji labarin mutuwar Alhaji Haladu sai yazo gidan gaisuwa, da shi da matarsa da yayan su guda biyu. Hadiza taji dadin zuwan sa sosai, saboda dama ta jima bata ga na gida ba tun shekaru biyu da suka wuce da daya wan nata Audu yazo shigewa shima ya shigo gurinta shida iyalinsa. Ta kai su dakin ta suka zauna suka yi mata gaisuwa tare da jajanta abinda ya faru. Anan Jabiru ya bar iyalin nasa suka kwana biyu tare da Hadiza da yayan ta sannan ya sake dawowa ya zauna da ita yace "yanzu Inna da Baffa sun mutu, Alhaji Haladu ma ya mutu, Menene kike so zaki yi yanzu?" Tayi shiru tana tunani sannan tace "ni ban sani ba, Ni ban taba yanke wa kaina hukunci ba. Yanzu tunda kazo kai zaka gaya min abinda zanyj" ya kalli su Safiya da suke gefe suna wasa yace "ki hado kayan ki ki taho mu tafi, kina da sauran yarintar ki wata kila Allah zai baki wani mijin sai ki sake yin auren ki" ta danyi tunani sai ta gyada kai da sauri "shikenan yaya, dama nima ba jin dadin zaman gidan nan nake yi ba, zamu hada kayan mu sai mu biku kawai" ya girgiza kai. kayan mu sai mu biku kawai" ya girgiza kai yana kallon ta yace "ki hada kayan ki nace ba ku hada kayan ku ba. Wadannan yara ba da su kika zo gidan nan ba, ki bar su a inda kika same su nan ne gidan uban su. Ke kadai ce nauyi na, da ke kadai zan tafi, su nauyin dangin ubansu ne, su zasu kula da su". Ta bude ido tana kallon sa sannan ta kalli yaran nata da suke ta wasan doki a tsakar daki, Safiya tana yiwa Khadijah doki Sauda kuma tana binsu a baya. Jabiru ya mike yace "zan kara kwana biyu a garin nan saboda ki samu ki shirya a nutse, jibi zan shigo in dauke ki mu tafi". Ya dauki sandarsa ya juya ya fita. Ta zauna ta dafe zuciyar ta tana kallon yaranta. Kamar yadda ta fada, bata taba yanke wa kanta hukunci ba a rayuwarta, sai dai duk hukuncin da aka yanke mata ta bi shi, yanzu kuma gashi an yanke mata hukuncin rabuwa da yayanta, yaran da basu da kowa kaf duniya sai ita. Ya zata vi ta tafi ta barsu? A gurin wa zata tafi ta barsu? Me zai faru da su in ta tafi ta barsu? Ita bata da ilimi, bata san abubuwa da yawa na rayuwa ba amma ta san cewa duk duniya babu abinda take so sama da wadannan yaran guda uku, 15 A 4 P 8:16 PM Kwana biyun nan haka tayi su cikin rashin jin da din zuciya, har sai da matar Jabiru da take tare da ita har lokacin tayi ta tambayar. take tare da ita har lokacin tayi ta tambayar ta abinda yake damunta amma sai ta dauka kewar mijinta ne, a rana ta biyun Jabiru ya dawo daukan su, ya fita da kayan iyalinsa da suka zo dasu ya dawo yace da Hadiza ina nata kayan? Ta girgiza kanta tana goge hawaye daga idonta tace "bazan iya rabuwa da su ba. Ba zan iya tafiya in bar su ba. In har na rabu da su to a cikin makara nake za'a kai ni kabari na, ko kuma sune a cikin makara za'a kai su nasu kabarin" ya kalle ta, ya kalli yaran da suke zagaye da ita suna rike da zanin ta amma duk da haka bai ji cewa ya kamata ya tafi dasu gabaki daya ba shi a iya fahimtar sa ta rayuwa gani yake yi yara, musamman yara mata dole ne su zauna a gidan uban su, a ganinsa haka shine dai dai. Yace "shikenan. Ki zauna tare da su din, amma ki sani in kina zaune a gidan nan tare da yaran nan babu namijin da zai aure kj" shi babbar damuwarsa akanta ita ce kar ta rasa mijin aure, Har zai tafi kuma sai ya dauko kudi daga aljihunsa a kulle a leda ya mika mata sannan ya juya ya tafi. Ta bishi da kallo tana tunanin ko zasu sake haduwa ko kuma shikenan? A ranar yadda Hadiza taga rana haka taga dare da yayan ta a gabanta tana lissafin yadda zata fara wannan rayuwar amma ta kasa yanke shawara. In ta kalli yarn ta tuna cewa yanzu dukkan nauyin su yana wuyanta sai taji toro ya kamata. In sun tashi da safe ma yanzu ita zasu ce ta basu abincin. ma yanzu ita zasu ce ta basu abincin karyawa, da rana ma haka, suturar sakawarsu makarantar su, magani in basu da lafiya, ga kuma overall tarbiyyar su. Ta kirga kudin da Jabiru ya bata "dubu goma" su kadai ne abinda ta mallaka a yanzu. Ta ina zata fara? Hayaniya ce ta tashe ta da safe da yake sai da assuba ta samu bacci, a cikin hayaniyar ta taji ana ambaton sunanta, ta mike da sauri taga yayanta su ma duk sun tashi suna kallon ta fuskokin su cike da toro. Ta kuma fahimci hayaniyar a kofar dakin ta ne, Ta tashi ta bude kofa tare da tura yayan ta baya tana kare su da jikinta yadda ko ma menene ita zai sama ba su ba. Matan gidan ne da yayan gidan mata wadanda basu koma gidajensu ba suke ta masifa. Kusan duk a lokaci daya suke maganganu amma ta tsinci was daga cikin maganganun nasu '"wallahi ba zamu yarda ba, abinda akayiwa baban mu ba za'a cigaba da yi mana shi ba" "tunda yan'uwan ta suka fara zuwa, Allah kadai ya san me suke kawo mata" "wanda yazo jiya ina kallo ya mika mata wani abu a leda, jikina kuma ya bani asiri aka kawo mata zata binne mana a gida mu ma ta mallake mu" Hadiza ta fara kokarin kare kanta "wallahi babu abinda suka kawo min, kudi ne kika ga ya bani", ya bani" Amma babu wanda ya saurare ta, aka jawo ta ita da su Safiya aka fito da su waje sannan aka fara watso musu kayan su wajen, tana kuka tana rokon mutanen nan amma basu barta ba, sai da makota da sauran yan unguwa suka shiga cikin maganar amma aka kasa sasanta su, su haushin duk abinda Alhaji Haladu yayi musu ne suke kokarin hucewa akan Hadiza da yayanta suna gain cewa sune sanadi, bayan su kuma a nasu bangaren basu da laifin komai musamman ma yaran. Daga karshe dai aka tafi gurin dagaci aka sanar da shi, ya aika aka kira su har yara mazan dan a sasanta su amma abu yaki yiyuwa sunce su ba zasu zauna da ita a gidan ba, a karshe dagacin yace to ai itama Hadiza ita da yayan ta suna da gadon Alhaji Haladu, dan haka ya umarci limamin unguwar su da yaje ya raba gadon Alhaji Haladu a bawa Hadiza nata ita da yayan ta dan su samu gurin zama da kuma abinda zasu rike kansu. Amma sai dai da aka zo rabon gadon sai babban dan gidan yaya Malam yace ai Alhaji Haladu duk ya siyar da kadarorinsa kafin rasuwar sa yay wa Hadiza da yaran ta hidima, yanzu abinda ya rage kawai shine gidan da suke ciki, Wannan ya sa gidan kawai aka raba a matsayin gado, shima kuma gidan su ka nemi cewa a fitar wa da Hadiza bangaren ta daga gefe dan basa son. Hadiza bangaren ta daga gefe dan basa son zama da ita. Shima kuma limamin sai yayi hakan dan in ba'a raba su din ba ba za'a samu kwanciyar hankali ba. 6 3 8:16 PM Hadiza da yayanta sun samu dakin soro, inda nan ne da dakin Alhaji Haladu, tare kuma da rabin soron dan su samu hanyar shiga dakin nasu. Dakin ciki da falo ne da bandaki a ciki, sai dai kuma matsalar shine dakin nasa yafi ko ina tsufa a gidan, ginin yafi na ko'"ina lalacewa. Amma duk da haka Hadiza taji dadin samun seclusion daga jama'ar gidan. Ta gyara dakin ta jera furnitures dinta da kayan sakawarsu da sauran tarkacen ta. Suna cikin gyaran kayan nasu ne suka ga anzo da kwano irin wanda ake rufi da shi an raba soron biyu dai dai yadda liman ya raba musu, wato hanyar ma ba zasu hada da su ba. Bata gama mamakin hakan ba sai ji tayi ana buga musu wani kwanon a windows din su wadanda suke tsakar gidan. Wannan ya sa dakunan nasu suka yi tsananin zafi tunda babu taga ko daya kuma kofar ma gashi an saka musu kwano an rufe inda iska zata shigar musu, Kuma tunda basu da kitchen zai ya zamana a kofar dakin su suke hada wuta suyi girki. Wannan shima ya taimaka gurin kara zatin dakunan. Farko sauran kudin hannunta suka fara cinyewa, daga nan ta koma daukan kayan dakin ta daya bayan daya tana kaiwa gurin dillaliya tana siyarwa a wulakance tana siya. dillaliya tana siyarwa a wulakance tana siya musu abinci. A haka har suka cinye duk samiru da kwallayen ta na aure, a lokacin ne kuma ta fita daga takaba. A lokacin da take lissafin inda zata samu wasu kudin ne Safiya ta kawo mata shawara "Baba Hadiza ki ringa dafa min wake da shinkafa ina yi miki talla, sai muke samun kudi muna ajiyewa" Sauda tace "nima zan ringa yin tallan, nima zan ¡ya" Khadijah tace "Baba Hadiza nima zan yi". Hadiza ta tsaya tana kallon su sai ta girgiza kai, "ba zan dora muku talla ba, in kun tafi talla ta yaya zan kula da ku? In wani abun ya same ku a can kuma fa? In kuna zuwa talla kuma a wanne lokacin ne zaku je makaranta?" Safiya tace "in mun dawo daga makarantar zamu ke zuwa tallan ai" Baba Hadiza ta sake cewa "ba za kuyi talla ba" sai kuma ta kara da cewa "ni zanyi. Zamu ringa yin abincin siyarwa ku ku tafi Makaranta ni kuma in tafi talla, a haka zaku yi karatu har ku girma kuje babbar makaranta ku samu babban aiki ku gina babban gida sai ku zo ku dauke ni ku kula da ni, yanzu amma ni ce zan kula da ku". Washegari ta kira dillaliya har daki ta sayi gadajen ta gida biyu tun na aure, ta sauke musu katifun kasa tace sun she su kwana, Kudin kuma da su tayi jari. Daga nan sana'ar wake da shinkafa ta fara, kullum zata shirya Safiya da Sauda su tafi makaranta ita kuma ta dafa wake da shinkafa ta goya Khadijah ta dauki abincin aka ta tafi bakin kasuwa da. dauki abincin aka ta tafi bakin kasuwa da tasha talla, su kuma in sun taso zasu zo suci abincin da ta ajiye musu sannan su yi wanke wanke su gyara musu dakin su sai su tafi makarantar islamiyya, kafin su dawo ita kuma ta dawo sai tayi musu wanki ta shanya akan langa langan kofar dakin su dan ko shanya ba'a yarda ta shiga cikin gidan tayi ba. Sannan tayo cefanen abinda zasu dafa gobe. In dare yayi kuma anan soron su suke shimfida tabarma su zauna suyi ta hira tana basu labarai, wani lokacin na babansu wani lokacin na nata yan uwan, wani lokacin kuma lissafin abinda take so su zama nan gaba. Farko ba sa samun wata riba, except that suna samu su ci abinci kuma jarin su bai karye ba, daga baya kuma sai Allah ya buda musu sana'a ta kankama sosai har jarin ya ishe su suka fara yin awara da daddare a kofar gidan. Tun a ranar da suka fara dora kaskon awara Dauda yazo wucewa ya gani yace "ba zaku mayar mana da kofar gida dandali ba, ko ku sauke kaskon nan ko kuma duk ranar da na kuma ganin sa in barar da shi". Safiya ta tashi zata yi masa rashin kunya Baba Hadiza ta hana ta, sai suka janye suka koma kofar gidan makota suke yi a can, Shekarun su biyu a cikin wannan yanayin, a cikin wadannan shekarun sun kuma shakuwa da junan su sosai, Basu da wani tension zasu ci su koshi sue makaranta kuma suyi wasa da junan su. Basu da kudi. kuma suyi wasa da junan su. Basu da kudi amma suna da junan su kuma suna gain su kadai sun isi kansu. 12 8 2 8:16 PM A lokacin ne wata rana suna tafiya a kasuwa zasu yi cefanen abincin siyarwar su sai Safiya ta ga gidan hoto "Baba Hadiza dan Allah mu shiga muyi hoto muma" Baba Hadiza tace "wanne irin hoto kuma dan bata lokaci? Muyi sauri mu tafi gida kar lokacin dora awara yayi azo nema bamu fara ba" Safiya ta kara rike hannun ta "dan Allah Baba Hadiza mu dauka, kinga yanzu Baba ko hoton sa bamu da shi". Wannan ya karyar da zuciyar Baba Hadiza, tabbas ko hoton Alhaji Haladu basu da shi. Sai ta amince suka shiga suka dauki hoton. Not knowing wannan hoton shine zai zama memory din su. The first tragedy struck shekaru biyu da yan watanni da rasuwar Alhaji Haladu, ranar Khadijah ta tashi da mugun zazzabi lokacin tana da shekaru shida a duniya, Baba Hadiza ta bata magani ta kwantar da ita a daki amma har su Safiya suka dawo daga makaranta zazzabin bai sauka ba sai ma zafi da jikin ya kara yi, aka sake bata wani maganin har zuwa washegari amma zazzabi bai sauka ba, a lokacin ne kuma suka lura cewa wuyanta ya sankare bata iya juyashi gefe, sannan kuma bata iya hadiyar abinci. Sai kuka take yi "Baba Hadiza wuyana ciwo yake yi, ki kaini asibiti" ta fada da kyar. yake yi, ki kaini asibiti" ta fada da kyar. Babu shiri Hadiza ta kaita chemist aka duba ta aka ce sai asibiti, suka je asibiti a take aka kwantar da su aka ce sankarau ce ta kamata saboda rashin wadatacciyar iska a dakin da suke kwana. Aka rubuta musu ma gunguna da allurai ga kuma kudin gado, babu shiri hadiza ta fasa bankin da take fara ribar sana'ar ta ta biya duk kudaden da ake nema. Kwanan su biyu a asibitin jikin ya sake ta'azzara aka tura su asibitin Gusau, a lokacin Khadijah ko magana bata iya yi. A can sai da duk abinda Baba Hadiza ta tara suka kare wajen magani, dama ba wani abun kirki ta tara din ba. Da kudin hannun ta suka kare ta shigo mota ta dawo Kura ta ringa bin gidajen yan uwa da yayan Alhaji Haladu akan su taimakawa yar uwarsu Khadijah su cece rayuwar ta amma babu wanda ya taimaka mata, haka ta ranci kudin mota a makota ta koma Gusau, kwanan ta biyu da komawa Allah yayi wa Khadijah rasuwa. Mutuwar Khadijah ta taba Baba Hadiza fiye da sauran mace macen da akayi mata, yayanta sune treasure din ta, zata iya bada ranta a saboda su amma ita mutuwa bata tambayar zabi wanda lokacin sa yayi shi take dauka. Su Safiya sunyi kuka kamar idanun su zasu fado kasa dan suna matukar kaunar kanwar ta su amma Allah ya fi su santa. Sai dai ta tafi ta bar wani rami a zukatansu wanda babu wani wanda zai iva cike shi. zukatansu wanda babu wani wanda zai iya cike shi. Daga nan kuma sai rayuwa ta komawa su Safiya baya, babu jari babu riba babu abinda za"a siyar a samu jarin sai tarin basussuka da suke kansu, ga kuma kewar Khadijah. A neme nemen jarin da Baba Hadiza take yi ne taje gidan Hajiya Kyauta. Hajiya Kyauta macece yar kasuwa, tana dillancin manyan kaya kuma tana kasuwanci zuwa garuruwa da yawa a Nigeria wani lokacin ma har kasashen waje take zuwa. Baba Hadiza ta nemi ta bata aron kudi ta sake tayar da jarin wake da shinkafar ta amma ita kuma sai ta nemi ta bata jinginar wani abu kafin ta bata jarin. Baba Hadiza ta gaya mata bata da komai sai tsofaffin katifun da suke kwana akai sai kuma kayan sakawar su. A lokacin ne Hajiya Kyauta ta bata shawara "kina da yammatan yara kamar wadannan, ki bani ko da babbar ne in tafi da ita wani garin in kaita aikatau, duk wata za'a ke aiko miki da kudin da zai isa ki kula da kanki ki kuma kula da karamar, ita kuma kin ga an dauke miki nauyin kula da ita" Baba Hadiza ta juya tana kallon Safiya da duk ta fita daga hayyacin ta saboda wahala, tace "aikatau kuma Hajiya, Satiya ba zata iya aikatau ba" Hajiya Kyauta tace "to ai koya zata yi. Na kai yara da yawa kuma sunyi arziki iyayen su ma haka. Baki san a inda arzikin ta yake ba" Baba Hadiza ya girgiza kanta "ba zan iya yi mata haka ba. Ba zan dora mata nauyin kula da ni da yar uwar. zan dora mata nauyin kula da ni da yar uwar ta ba. Ni ce mahaifiyar ta. Ni zan kula da ita. In aikin ne ma ni ki nema min in ringa yi ina samun kudi ina kulawa da su". 14 5 8:16 PM Hajiya Kyauta tace "to ai in dai zan dauke ki in tafi da ke sai dai ki barsu anan ke nan. Kina da wanda zaki barwa su?" Hadiza tace "bani da kowa sai Allah. In kina da hanya dan Allah ki samar min aikatau din anan garin yadda ba zan rabu da su ba. Sai in ringa yin aikin ina tara kudi har in samu jarin da zan dawo da kasuwanci na". Haka ce ta kasance, aka samo wa Baba Hadiza aikatau take yi a gidan wasu masu hannu da shuni, kullum da safe su Safiya zasu fita makaranta ita kuma zata tafi gurin aikin ta bayan ta dafa musu abinci ta ajiye musu, in sun dawo zasu ci abinci suyi ayyukan su a gida sannan su taflislamiyya, da daddare zata dawo ta taho musu da abinci daga can. Albashin ta dashi suke samu suke cin abinci da kudin sabulun wanka da wanki da littattafan makaranta, dan duk talaucin su Baba Hadiza ba ta yarda sun daina karatu ba, Suttura kuma mostly kwance ake basu a gidan aikin ta da kuma makotan su, A haka suka sake yin wasu shekaru biyun, Baba Hadiza ta dan tara jari kadan sai ta dawo da yin awarar dare tunda da rana tana gidan aiki babu damar tallan wake da shinkafa. A lokacin ne kuma second traaedv va faru. wake da shinkafa. A lokacin ne kuma second tragedy ya faru. Lokacin Safiya ta yi jarabawar kammala primary school, Sauda kuma tana aji hudu. Kamar kullum sun dawo daga islamiyya suka yi sallar magrib sannan suka fito waje suka hada wuta suka fara suyar awara kafin Baba Hadiza ta dawo. Suna cikin yi Dauda yazo wucewa ya tsaya yana kallon su yace "bana hana ku kafa mana dandali a kofar gida ba?" Basu kula shi ba kamar yadda Baba Hadiza tayi musu umarni, ya sake cewa "shegu yayan kaddara, baba dai ya cuce mu da ya hada mana jini da ku. Gadon talauci" still basu kula ba duk kuwa da irin zuciyar da take cin Safiya. Ya sake cewa "ina uwar taku take ne wai? Ko bata dawo daga karuwancin ba?" A lokacin ne gabaki dayan su suka mike suka yi kansa, dama haka yake bukata, ya damki wuyan su duk su biyun ya shake a lokaci daya. Wani yaro dan makotan su da yazo siyan awara ya ruga da gudu hanyar da yasan Baba Hadiza tana tahowa, a hanya ya ganta "Baba Hadiza ki zo Dauda zai kashe su Sauda. Ta yar da abincin hannunta, abincin ta na rana da ta ajiye musu zata kawo musu suci da daddare, sannan ta ruga da gudu ta sha kwanar da zata kai ta inda yayan nata suke, a dai dai lokacin da wata mota ta sha kwana ita ma a guje, Akan don Safiya motar ta daki Baba Hadiza, akan idonta kuma Baba Hadizan tayi sama. ta na rana da ta ajiye musu zata kawo musu suci da daddare, sannan ta ruga da gudu ta sha kwanar da zata kai ta inda yayan nata suke, a dai dai lokacin da wata mota ta sha kwana ita ma a guje. Akan idon Safiya motar ta daki Baba Hadiza, akan idonta kuma Baba Hadizan tayi sama sannan ta fado direct akan titi a gaban motar. Ta fincike daga hannun Dauda tare da kurma ihu ta fita a guje gurin da mahaifiyar tata ta fadi, sai dai tun kafin ta karasa ta sani har cikin zuciyarta cewa Baba Hadiza ta tafi ta barsu. Maman Maama (a) 28 27 10 6 8:16 PM. EPISODE TWENTY ONE owner 17 edited 8:42 PM Safiyya LTE • Episode Twenty One : The Tragic Family 2 Paid Advert *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad.* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*, *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332*. Ta karasa gaban Baba Hadiza tana kallon ta tana mayar da numfashin gudun da tayi, a daidai lokacin da Sauda ta karaso ita ma a guje tare da rike hannun yaruwar tata, sai kuma ta saki hannun ta durkusa a gaban baba Hadiza ta rungume ta "wayyo Baba Hadiza wayyo Allah na" a take jinin da yake fita daga kan baba Hadiza ya wanke kayan jikin Sauda. Safiya ta tsaya tana kallon su bata ce komai ba, a dai dai lokacin da mutane suka fara taruwa a gurin suna ta salati, a cikin mutanen ne Safiya taga yaya Malam ya zo wucewa shima ya leko yana son ganin abinda ya faru, tayi gurinsa da sauri, desperate to get any kind of help for her dying mother, ta kama kannunsa "Yaya Malam dan Allah ka taimaka mana, dan Allah kazo ka taimakawa Baba Hadiza" ta fada cikin rawar murya da karyewar zuciya. Ya yarfar da hannun ta yana goge nasa hannun a jikinsa kamar wadda ta shafa wa kashi, "kar ki kira sunana ki shafa min kashin kaj, taimakon me zanyi muku? Ni na kade ta? Ba zanje inyi bayani a gurin yan sanda ba wallahi" sai ya juya da sauri ya bar gurin, sai a lokacin ta lura bayan shi akwai yayyensu wadanda suke uba daya su uku a wajen, amma duk cikin su babu wanda ya taimaka musu ko da kuwa ta hanyar gaya musu magana mai dadi ne, Mai motar ne yazo a rikice ya daga Baba Hadiza daga jikin Sauda wadda gabaki daya ta gama rikicewa, sai da Safiya ta rike ta sannan aka saka Baba Hadiza a mota suma. sannan aka saka Baba Hadiza a mota suma sula shiga aka tafi da ita asibiti. Haka Safiya ta zauna a mota hannayenta biyu rije da na Baba Hadiza, idanuwan ta akan fuskarta. A ranta ta san ta mutu, amma zuciyar ta taki yarda tayi accepting, so take taga ta motsa, so take taga ko da fatar idonta ce ta motsa, so take taji ta rike hannun ta kamar yadda ta rike nata. Amma baba Hadiza motsi ya riga ya kare. Sai sanyi ma da hannun nata yake karayi with each passing second. Gwajin farko da akayi a asibiti aka tabbatar da cewa ta mutu. Sauda ta kara rilicewa "ka sake dubawa, ba ka duba sosai ba, ta ji cimo ne kadai shi yasa ta suma, suma tayi shi yasa bata motsawa. Ku barta zata tashi. Likita ka sake dubata". Safiya tana nata kukan tana kuma rarrashin Sauda, daga baya sai suka rungume junansu a gaban gawar mahaifiyarsu jikin su jike da jininta suna kuka. Duk wanda yake gurin sai da yayi musu kuka tun daga kan drivern motar har zuwa likitan da sauran majinyatan da suke gurin. A daren aka dawo da gawarta gida, makota da abokan arziki ne suka yi mata suttura anan dakin ta a gaban yayanta, sai da aka gama shiryata ma sannan matan Alhaji Haladu suka fito, Inna Sa'ade tace ita ba ta ma ji labari ba sai a lokacin, ita kuma inna Gaje tace ciwon kafa ne yake damun ta shi yasa bata samu damar fitowa ba. Sai da akayi sallar asuba sannan aka fita da. akayi sallar asuba sannan aka fita da gawarta akayi mata sallah. Aka kuma dauketa zuwa gidanta na karshe. Baba Hadiza ta mutu tana da shekaru ashirin da takwas a duniya, ta mutu shekaru hudu bayan mutuwar Alhaji Haladu. A lokacin Safiya tana da shekaru goma sha uku Sauda kuma tana da sha daya. Ana tafiya da ita Sauda ta juyo gurin Safiya idanuwan ta cike da toro tace "Safiya, dan Allah kar ki mutu ki barni, bana so ku barni ni kadai a duniya". Mutuwar Baba Hadiza ita ce worst experience na rayuwar Safiya, duk wanda ya san ta ya san har ta koma ga Allah bata warke daga jimamin mutuwar mahaifiyar ta ba. Daga nan Safiya da Sauda suka bude wani sabon babi a rayuwar su. Kowa ya tausaya musu tabbas, duk wanda yazo gaisuwa zai shafa kansu yace "Allah sarki yaran nan abin tausayj" amma babu wanda yace "ku dawo gurina ku zauna zan rike ku" saboda babu wanda yake son responsibilities. Tail 19 14 10 2 2 8:47 PM Kawu Haruna, wani kanin Alhaji Haladu da yake da rai a lokacin shi ya fara gudun responsibility dinsu lokacin da yaga ana kokarin lika masa. A gurin zaman makoki yaji. akayi sallar asuba sannan aka fita da gawarta akayi mata sallah. Aka kuma dauketa zuwa gidanta a karshe. Baba Hadiza ta mutu tana da shekaru ashirin da takwas a duniya, ta mutu shekaru hudu bayan mutuwar Alhaji Haladu. A lokacin Safiya tana da shekaru goma sha uku Sauda kuma tana da sha daya. Ana tafiya da ita Sauda ta juyo gurin Safiya idanuwan ta cike da toro tace "Safiya, dan Allah kar ki mutu ki barni, bana so ku barni ni kadai a duniya". Mutuwar Baba Hadiza ita ce worst experience na rayuwar Safiya, duk wanda ya san ta ya san har ta koma ga Allah bata warke daga jimamin mutuwar mahaifiyar ta ba. Daga nan Safiya da Sauda suka bude wani sabon babi a rayuwar su. Kowa ya tausaya musu tabbas, duk wanda yazo gaisuwa zai shafa kansu yace "Allah sarki yaran nan abin tausayi" amma babu wanda yace "ku dawo gurina ku zauna zan rike ku" saboda babu wanda yake son responsibilities, Ta 19 14 10 2 2 8:47 PM Kawu Haruna, wani kanin Alhaji Haladu da yake da rai a lokacin shi ya fara gudun responsibility dinsu lokacin da yaga ana kokarin lika masa. A gurin zaman makoki yaji. kokarin lika masa. A gurin zaman makoki yaji ana zancen cewa shi ya kamata ya dauki yaran. Nan da nan sai yayi dabarar fara furta maganar yace yaya Malam ne ya kamata ya daukesu '"sai ka hada su da yaran gurin ka sa'anninsu" yaya Malam yace "haba kawu, ni yanzu nawa iyalin ma da yaya nake rikon su ballantana in karawa kaina da wasu?". Daga nan sai magana ta fara, aka ringa tayin su a cikin dangi kamar wasu kaya kowa yana cewa baya so. A karshe dai su manyan mazan suka dage lallai sai dai a bar su anan gidan Inna Sa'ade ta dauki daya Inna Gaje ta dauki daya. Suma farko suka ce ba zasu dauka ba sai da aka hada da magiya sannan suka dauka. Inna Gaje tace "dama ai tun sanda Alhaji ya gaya mana zai yi sabon aure zai auri yarinya sai da muka gaya masa cewa ba zai auri yarinya karama ta zazzaga yaya shi kuma gashi girma ya dame shi a karshe ya barmu mu da yayan mu da rikon yayan da bamu muka haifa ba, gashi nan kuma hakan ta faru" Inna Sa'ade tace "haka kawai mu ba da haihuwar yaya ba yanzu an barmu da raino, mum gama rainon namu yayan lokacin da zamu huta yazo amma za'a kawo mana wani rainon da ban" yaya Malam yace "Inna ai ba rainon su zakuyi ba, yaran nan babu wacce ba zata iya kula da kanta ba, kawai dai su zauna a gurin ku in kunyi abinci ku zuba musu, shikenan fa, kuma kuma ai zaku more su tunda zasu ke taya ku aikin gida". Wannan ne ya saka suka yarda suka dauke su din, ba wai dan Allah ko dan suna so ba, su din, ba wai dan Allah ko dan suna so ba, saboda su taya su aikin gida, amma kuma aikin sai ya wuce na tayi ya koma na bauta. Dakunan gidan gabaki daya su suke sharewa, duk girman tsakar gidan nan shima su zasu share shi suyi wanke wanke suyi wankin kayan matan gidan saboda idan basu yi musu ba ba zasu basu sabulun da zasu wanke nasu kayan ba. Sai dai kuma a zahiri kusan dukkan aikin Safiya ce take yinsa da Sauda tun da Baba Hadiza ta mutu bata dawo cikin hayyacin ta ba. Ko yaya aka danyi motsi da wani abu sai ta tsorata, ko yaya aka yi mata magana sai ta firgice, kusan kullum kuma a cikin kuka take. Amma babu wanda yake kulata ko da kuwa da magana mai dadi ce, in tana wannan girgitar ma sai Inna Sa'ade tayi ta fada tace ita an hada ta da rikon mahaukaciya. Haka Safiya zata wuni tana aiki tana kuma rarrashin Sauda duk kuwa da cewa ita ma tata zuciyar a karye take, amma in tace ita ma zata zauna tayi ta kuka wa zai kula da Sauda kenan? Babu wanda yayi maganar komawar su makaranta ita ma kuma safiya bata yiwa kowa maganar ba dan ta san in ma tayi fada kawai za'a yi mata kuma ba kai ta za'a yi ba, musamman tunda sabuwar makaranta zata shiga dole sai an dinka mata uniform an siya mata books, Sauda kuma a yanayin da take ciki a yanzu bata jin zata iva zuwa makaranta, Watannin su hudu a hannun Inna Sa'ade da Inna Gaje, azaba iya azaba sun shata a cikin. Inna Gaje, azaba iya azaba sun shata a cikin watannin nan, reward din aikin bautar su kawai shine abinci da sabulun wanka, dan na wanki ma sai dai in Safiya ta wanke wa matan gidan nasu ta saka nasu kayan a cikin ta wanke musu suma. Bayan wata hudun ne ranar nan Safiya tana kwance a kan tabarmar da ake bata tana kwana a dakin Inna Gaje ta jyo kukan Sauda a tsakar gida, ta mike da sauri tana laluben hanya saboda duhu ta fita tsakar gida tana kiran sunan Sauda, ta amsa mata ita ma tana laluben ta har suka hadu a tsakiya. Ta rungume ta tana jin yadda jikinta yake karkarwa tace "Sauda me kike yi a waje, a cikin duhun nan?" Sauda tana kuka tace "Inna Sa'ade ce ta koro ni waje, na kasa bacci, toro nake ji, shine nake yin kuka, shine ita kuma ta koro ni waje". Safiya ta rungume ta "shikenan ya isa haka, ki daina kukan, gani nazo taho muje mu kwanta" ta ja ta zuwa dakin Inna Gaje inda take kwana, suna zuwa zasu shiga Inna Gaje ta haska su da fitila, ashe idonta biyu taji kukan Sauda kuma ta ga sanda Safiya ta fita, tace "mayar da ita inda kika dauko ta, wallahi ba za'a kara min wahala ba, ba zaki kawo min wanna mahaukaciyar yarinyar daki na ta hana ni bacci ba" Sauda ta kara saka kuka tana kankame Safiya "Safiya tsoro hake ji, kar ki. tafi ki barni" Safiya tana bubbuga bayan ta tace "babu inda zan je, taho mu je mu kwanta a dakin mu". A haka cikin duhu suka laluba suka tafi soro sannan suka tura dakin Baba Hadiza suka shiga, suka lalubi tsohuwar katifar su suka kwanta akai tare da kankame junan su, a haka bacci ya dauke su. Washegari suka tashi da gyaran dakin Baba Hadiza, suka fitar da katifun waje suka share suka wanke bandakin sannan Safiya ta hada duk wani abu da tasan zata iya siyarwa irin su tsofaffin kwanuka da tukwane ta kaiwa yan gwangwan, kudin da suka bata ta auno waken soya ta dawo da sana'ar awarar da suke yi da, dama kaskon ta da sauran kayan aikin ta suna nan. Kullum in ta gama bautar aikin gida, da yamma kuma zata soya awarar ta a kofar gidan makotan su, da daddare kuma zata rungume kanwarta suyi bacci du kadai a dakin soro, Babu wanda ya tambaye su me yasa suka dawo dakin, babu kuma wanda suka yi wa bayani, Sai dai aikin bautar cikin gida har lokacin bata daina shi ba, zata yi musu aikin zasu bata abincin rana kadai, wani lokacin da daddare tana kallon abincin zasu kira almajirai su basu amma su ba zasu basu ba, Nan da nan sai sana'ar awarar ta ta kara habaka, da ribar suke cin abincin safe da ita. habaka, da ribar suke cin abincin safe da ita kuma ta hada ta siya wa Sauda littattafai tace ta cigaba da zuwa makaranta. Sauda tace "ke kuma fa? Ke ba zaki koma makarantar ba?" Safiya tace "in Allah yayi ina da rabon yi sai ki ga nayi watarana. Yanzu ke zaki yi. Kiyi karatu sosai har ki tafi kasar waje ki hadu da turawan Ingila" suka yi dariya tare sannan Sauda tace "ina kewar Baba Hadiza. Ina so in ganta in gaya mata kina kulawa da ni". A haka rayuwa ta cigaba, da safiya ta ga kudin awara baya isar su sauran bukatun su sai ta kara wa kanta wata sana'ar, ta shiga gidajen makota ta gaya musu cewa ta iya kitso, idan suna son kitso su ringa zuwa tana yi musu suna biyan ta. Daga nan sai ta kara da wanki, wankin kayan yaran makota duk wanda ya ke so ya kawo ta wanke masa ya biya ta kudi. A haka a haka Safiya har suttura take sia musu ita da Sauda, Sauda ta kan taya ta da wankin in an kawo, da daddare kuma ta taya ta da suyar awara. Gabakidaya safiya ta fita daga cikin hayyacin ta, ta rame ta zama sai kashi, dogon gashinta duk ya lalace ya diddige saboda wahala, in ka ganta zaka dauka tafi karfin shekarun ta. Ta san yadda zata samu kudi, ta san yadda zata yi budgeting su sayi abinda yake da muhimmanci su bar wanda bashi da shi. Kullum zata wuni cikin wahala, in dare yayi kuma ta rungume kanwarta suyi bacci su kadai a dakin soro. Wannan ya kara musu matsananciyar shakuwa da junan su. bacci su kadai a dakin soro. Wannan ya kara musu matsananciyar shakuwa da junan su. Watanni takwas bayan nan, lokacin da aka yi shekara guda da rasuwar Baba Hadiza, a lokacin ne babban dan Inna Sa'ade da yake Kano yake kasuwanci yazo ya sa aka rushe bangaren babar ta sa aka yi mata ginin bulon siminti. Kafin ayi ginin sai da aka yi ciko sosai dan dakuna suyi sama, sannan aka jingina katangar ginin a jikin dakin da su Safiya suke kwana aka rangada wa Inna Sa'ade dakunan ta na bulon siminti manya manya guda uku da kitchen din ta da bandakin ta. A lokacin da aka gama ginin ne, a lokacin kuma damuna ta sauka. Tunda damunar ta sauka kusan duk ranar da aka yi ruwa dakin su cika yake yi da ruwan sama, a lokuta da dama sai dai su fito soro su kwanta har sai an gama ruwan sannan su kwashe wanda ya taru su koma ciki. Tun Safiya tana daurewa har dai ta samu Inna Sa'ade tayi mata maganar, sai ta bita da mugun kallo tace "to yanzu ya za'a yi? Ko kiran sa zanyi in gaya masa ga daya uwar ta sa nan bai yi mata sabon gini ba ita?" Haka Safiya ta hakura ta bar maganar, a yarintar ta ita damuwar ta shine ruwan da yake lalata musu kaya kuma yake hana su bacci, bata hango babban al'amarin da ruwan zai jawo ba, A lokacin ne tragedy na uku ya saukar wa Safiya. Tragedy din daya karasa tarwatsa. Safiya. Tragedy din daya karasa tarwatsa zuciyar ta, ya kuma mayar da ita ya hade ta zama tamkar dutse. 10 5 3 1 8:47 PM A wani daren litinin kamar kullum bayan sun kwashe kayan suyar awarar su sun kai daki, suka kunna yar karamar fitilar su suka ajiye, sannan suka yi shirin kwanciya bacci, suka kwanta rungume da junan su suna hira, hirar Baba Hadiza da irin burukan ta akan su, hirar Khadijah da surutun ta, da kuma hirar rayuwar su a yanzu. "ni dai Safiya bana so mu rabu, ko kin girma kin yi aure ma sai na biki gidan ki, duk inda zaki je sai na biki" Safiya ta ce mata "babu inda zanje ai na gaya miki. Kuma ni ba zan yi aure ba. Zan zauna da ke har sai kin gama karatun ki, kin samu aiki kin gina babban gida sai ki zo ki dauke ni muje mu zauna tare" Sauda tayi dariya "ina kewar Baba Hadiza. Ina so inje gurin ta" suka yi shiru sai kuma tace "ni kuma so nake in kin kara girma kin yi aure kin haihu, ina so yar da zaki haifa ta zama duk abinda Baba Hadiza take so mu zama. Ta zama yar gayu mai tuka motoci masu kyau, ta zama mai ilimi da turanci kamar baturiyar ingila, sannan ta zama kyakkyawa kamar Baba Hadiza" Safiya ta jawo ta ta kwantar da ita tace "duk ke zaki zama haka, Zan cigaba da yin wankau da suyar awara har sai kin zama haka" Sauda ta rungume ta tare da cusa fuskarta a wuyan ta tace "bacci zanyi yanzu, na daina jin toro yanzu. Kiyi mana addu'a. Sai da safe" safiya tace "to. mana addu'a. Sai da safe" safiya tace "to shikenan. Kiyi baccin ki. Sai da safe" sannan ta karanta adduoin kwanciya bacci ta shafa musu. Da assubar fari Safiya ta farka. Amma ba wai kiran sallar asuban ne ya tashe ta ba. Ji tavi kamar ana kiran sunan ta cikin baccin ta, ta zare hannun Sauda daga jikinta ta mike zaune, sannan kuma ta tashi tsaye ba tare da ta san me take yi ba. Ita ba ido biyu ba ita ba a farke ba. Kamar mai sleepwalking. Ta bude kofar dakin ta fita sannan ta cigaba da tafiya ba tare da tasan inda take saka kafarta ba. Sai da ta kai tsakiyar tsakar gidan su sannan taji wata kara daga bayanta "yif!" Karar da ta farkar da ita daga baccin da take yi, sannan kuma lokaci daya tun kafin ta juya bayan nata jikin ta ya bata abinda ya far sannan kuma zuciyar ta ta tabbatar mata da cewa Sauda ma ta tafi ta barta. Ta juya da sauri ta kalli dakin da ta fito daga ciki just few seconds ago, tun daga cikin dakin har falon har toilet din har soron gabaki daya katangunsu sun afka ciki, sun fada akan Sauda, Tayi wata irin kara wadda gabaki daya unguwar babu wanda bai ji ta ba, sannan ta fita a guje ta hau kan tarin kasar ta fara kokarin daga kanukan rufin da suka rufe kasar, Kusoshi biyu ta taka a lokaci daya amma babu wadda taji zafin shigar ta cikin kafarta, Kuka take yi da iyakacin karfin ta. kafarta. Kuka take yi da iyakacin karfin ta tana kiran sunan yar uwar ta "Sauda, kar ki tafi ki barni", Makota ne suka fara shigowa, wadansu dama already sun tashi da niyyar zuwa masallaci, daga baya jama'ar gidan suma suna fito, da kyar aka samu wani makocin su ya rike Safiya, hannayensa biyu ya saka ya rike ta gam a jikinsa yana tofa mata adduoi sannan aka samu ta nutsu ta tsaya a guri daya yayin da matasa suka hau aikin hakar kasar. Gini ne irin na da katangar mai kauri ce sosai gashi ta sha ruwa dan haka suma mazan da kyar suke dauke ta. Ba'a samu tono Sauda ba har sai da gari ya waye rana ta fito sosai. Tun kafin a dauko ta dama duk wanda yake gurin ya fitar da ran samun ta da rai. Sanda aka fito da gawar ta shi kansa wanda yake rike da Safiya gagara sa tayi. Tayi kan Sauda tana wani irin kuka mai ratsa zuciyarsa da ruhin duk wanda yake sauraronta. Ta rungume ta kamar zata tsaga kirjinta ta saka ta a ciki. "kar ki tafi ki barni, dan Allah kar ki barni ni kadai" A ranar hatta yan'uwan Safiya da basa ga maciji da ita sai da suka zubar mata da hawaye, Da kyar aka banbare gawar Sauda daga jikin Safiya aka yi mata suttura aka yi mata sallah aka dauke ta a makara zuwa gidan ta na gaskiya, A lokacin da ake fita da gawar kowa a gidan kuka yake yi, ba kuma wai kukan mutuwar Sauda ake yi ba ko kuma kukan sabo da ita ba, kukan tausayin Safiya ake yi, da yawa mutane sun dauka ba zata yi rai ba, sun dauka bin yaruwar tata zata yi. ake yi, da yawa mutane sun dauka ba zata yi rai ba, sun dauka bin yaruwar tata zata yi. A lokacin mutane da yawa sun fadi albarkacin bakin su akan dalilin faduwar dakin da kuma mutuwar Sauda 6 8:47 PM '"wannan sabon ginin da akayi shi ya kashe dakunan" "to da ya akayi ma aka barsu suke kwana a wannan gurin su kadai?" "Ai ruwan cikin gidan gabaki daya cikin katangun dakunan yake shiga" Amma kuma babu wanda ya daga maganar ballantana har a dauki matakin shari'a akai. Daga nan Safiya ta sake bude wani yet another page na rayuwa. She became totally depressed, ta daina cita daina sha ta daina wanka ta daina magana da kowa, babu abinda ta so a lokacin kamar mutuwa, da ana siyan mutuwa da tabbas zata nemi kudi ta siya wa kanta, Ta koma dakin Inna Gaje da kwana, tunda bata da wani gurin zuwan idan ba can din ba, ita ma kuma Inna Gajen ta dan sassauta mata yanzu dan bata saka ta aikin komai kuma ko ta saka tan ma babu tabbas din cewa zata yi. Wata daya bayan nan tana kwance a inda. Wata daya bayan nan tana kwance a inda take kwanciya kamar kullum taji shigowar yaya Malam, yazo ya shige ta ya shiga gurin mahaifiyar ta sa a gaishe ta sai safiya taji Inna Gaje tace "dama jira nake kazo, gwara ka san yadda zaka yi da yarinyar can kar ta mace min a daki azo a barni da salati" yace "me ya same ta?" Tace "bata ci bata sha, yadda ka ganta din nan a kwance haka take wuni take kuma kwana. Ni fa ba zanyi jinyar ta ba. Ku da take yaruwarku ubanku ya bar muku wahala sai ku san yadda zakuyi da ita, ni nayi na Allah kuma na gaji haka". Yaya Malam yace "to Inna ni ai bani kadai ne yayan ta ba, dan ina babba shikenan komai sai ace ni? Ba ga su Namadi nan ba su da suke birni ai sun fi ni arziki" Inna Gaje tace "to ai ba zasu yi ba, in ta mutu kuma ba za'a zage su ba kai da aka sani kai za'a zaga. Dole ka san yadda zaka yi da ita" Yayi shiru sannan yace "na san me zanyi a kanta. Ni ba zan kaita gida na ba wallahi in yi ta rigima da iyali a kanta. Aure zanyi mata. kwai tsohon hedimastern mu da yayi retire kwanan baya, dama ya taba yi min maganar ta yace ko zan bashi ita sai na mayar da maganar wasa, gwara inyi mata auren kawai in taje gidan mijin zata warke a can. Gobe in na hadu dashi zanyi masa magana in har yanzu yana son ta yazo kawai ay" Inna Gaje tace "hakan ma yayi, Kace masa sadaki kawai zai kawo ba sai yayi hidimar komai ba in yaso sai yayi mata kayan daki, dan babu abinda zamu siya mata" yace "sai. dan babu abinda zamu siya mata" yace "sai ta je itama tayi irin zaman da uwar ta tayj" Baba Gaje tace "to Allah ya sa dai kar a maimaita, kar taje ta kwantsama yaya shima ya mutu ta debo yayan ta sake dawo mana nan". Safiya ta bude idonta, sannan ta tashi zaune tana kare wa dakin kallo sai kuma ta mike tana jin kamar kafafuwan ta ba zasu dauke ta ba. Waje ta fita, taje ta hau kan tudun kasar da yake nan ne dakin su a da, inda tayi rayuwa da iyayen ta da yan'uwan ta. Ta kwanta ta sake rufe idonta tana jin iskar damuna tana kada ta, tana shakar kamshin kasar da take kwance akai. Anan ta yanke hukunci. Anan ta bude sabon babi a rayuwar ta. Ta mike kafarta ko takalmi babu tana tafiya iska tana yawo da ita, tiryan tiryan ta taka har gidan da tayi niyyar zuwa, gidan Hajiya Kyauta. Hajiya Kyauta tana zaune a tsakar gidan ta sai gain yarinya tayi kamar aljana ta shigo mata, kafarta da ciwon kusar da ta taka garin tono gawar yaruwarta, Hajiya kyauta ta mike a tsorace, sai kuma ta tsaya tana kallon yarinyar ta a tunanin a inda ta san fuskarta, Safiya tace "sunana Safiya, Dan girman Allah ina so ki taimaka min" sai a lokacin Hajiya Kyauta ta gane ta, ta koma ta zauna tare da cewa "ke ce yarinyar nan Safiya yar gidan marigayiya Hadiza, bana gari ta rasu, sai da na dawo sannan aka bani labarin. da na dawo sannan aka bani labarin abinda ya faru da ita. Ina yaruwar ta ki?" Safiya tace "ta mutu, duk gabaki dayan su sun mutu. Ni kadai na rage. Ni kadai suka bari", Hajiya Kyauta taji wani iri a zuciyar ta, yanayin yarinyar kadai ya isa ya bawa mutum tausayi ballantana abinda ta fada, tace "Allah sarki. Allah mai iko. Yanzu to ni me kike so in taimaka miki da shi? Abinci kike so ko kudi?" fan 11 2 1 8:47 PM Safiya ta girgiza kanta "so nake ki dauke ni daga garin nan. Bani da sauran abinda zanyi a garin nan. Bani da iyaye bani da yan uwa bani da kakanni, ban san dangin uwata ba dangin ubana kuma basa so na, aure suke so suyi min, so suke yi in maimaita rayuwar wahala irin wadda Baba Hadiza tayi, so suke yayan da zan haifa su maimaita rayuwar wahala irin wadda ni da yanuwana muka yi. Ba zan yarda hakan ta kasance da ni ba. Ba zan bari hakan ta kasance da ni ba. So nake ki kaini garin da zanje in nemi kudi, kudi nake so inyi irin wanda yayan da zan haifa ba zasu taba fuskantar rayuwa irin wadda na fuskanta ba, kudi nake so in yi yadda ni ce zan zamanto mutum ta karshe a zuri'a ta da zai san dacin talauci", Hajiya Kyauta tayi shiru tana kallon yar yarinyar da take gabanta tana kuma jin yadda take zarar magana kamar wadda kae yiwa wahayi. Tace "ke yarinya ce Safiya. Shi arziki da talauci ai duk na Allah ne shine kuma yake rabawa ga wanda yaso" Safiya. kuma yake rabawa ga wanda yaso" Safiya tace "Allah kuma shine ace mu roke shi zai amsa mana, zan roke shi ya bani, na kuma tabbatar zai bani din". Kyauta tace "to ke yanzu kima da jari ne? Da me zaki nemi kudin?" Safiya tace "bani da jari, amma ina da rai na ina kuma da lafiya ta, da su zan nemi jarj". Hajiya Kyauta ta sake yin tunani tace "kina da rai da lafiya amma baki da karfi. Da ke namiji ce sai in kai ki Kano can ne cibiyar kasuwanci, sai in kai ki kiyi dako da laburanci ki samu jari" ta juyo tana kallon Safiya tace "amma ke macece, yarinyar mace. Aikatau zan kai ki gidan masu kudi, Abuja zan kai ki a can masu kudin suke. Suna bada albashi kuma mai kyau in dai zakiyi musu aiki mai kyau. Tunda baki da nauyin kowa kinga zaki tara kudin ki ne kawai. Daga nan zaki samu jarin da kike nema" tayi shiru tana cigaba da kallon Safiya, sai ta sake cewa "gidan Hajiya Maryam zan kai ki. Yar kasuwa ce sosai kuma bata da matsala, Zata baki ci da sha da sutura da magani kuma zata baki albashi, Sannan zaki koyi dabarun kasuwanci idan kina zaune da ita, Sai dai akwai yarjejeniya da zamuyi ni da ke" Safiya ta gyara zama tace "kome kike so in dai ina da damar yi miki zanyi mikj" Hajiya Kyauta tace "bana bukatar ko kwandalar ki, zan taimaka miki ne saboda girman Allan da kika hada ni da shi. Amma idan yan uwanki suka kama ki kina kokarin gudu, ko kuma bayan kinje can suka. ko kuma bayan kinje can suka gano inda kike, babu sunana a cikin maganar, bana son shiga cikin rigima". Safiya tayi murmushin takaici tace "ba zasu neme ni ba ko sunga bana nan. In sun gano inda nake ma kuma ba zan dawo ba. In na bar garin nan na bashi kenan har abada".[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: . EPISODE TWENTY TWO owner 12:54 AM Safiyya Episode Twenty Two: A Green Snake Bara mu bar Safiya ta huta haka nan...... Let's go back to Fiyya Naga kunyi missing Malam Muhammadu da "'Yaya, Yaya, Yaya!" Naji ana fada ana kuma jijjiga ni. Duk da ban gane muryar me magana ba amma na san mutun biyu ne duk duniya suke ce min yaya, either Hassan ne ko Hussain. Nayi kokarin bude ido a amma sunyi min nauyi da yawa, naji ina jin haushin ko ma wanene yake kokarin tashina, I wanted to go differ into tunanin Ammi na da yanuwanta, maybe watakila in nazo gurin da take tafiya ta barni zata tafi dani wannan karon, Naji an sake taba ni, wannan karon kuma muryar macece, muryar Mommy "Safiyya? Bude idonki ki kalle ni, talk to me" na bude ido na kamar yadda tace amma dishi dishi nake ganin ta, na bude baki zanyi mata. nake ganin ta, na bude baki zanyi mata magana kamar yadda tace amma sai bakin ya furta "Baba Hadiza" ta kalli wanda yake kusa da ita? Zaka iya daukan ta, go and look for someone ko Mustapha" "Mustapha yana gurin Daddy" ya amsa mata "Daddy " na maimaita sunan. Naji an dauke ni, naji kuma an saka ni a mota, daga nan sai maganganun mutane mostly muryar Mommy ce tana fada duk da ban san me take cewa ba. Sanda na dawo hayyaci na a asibiti na samu kaina, a kwance akan dago da ruwa a jiki na. Na kare wa dakin kallo sai naga Daddy a gefe a zaune akan electric wheelchair dinsa da dan karamin Alqur'ani a hannunsa. Na jima ina kallon sa kafin ya fahimci na farko sai ya rufe qur'anin ya karaso kusa da ni. "hey there" na kirkiri murmushi "hey" "ya jikin? Akwai inda yake miki ciwo ne?" Kusan komai na jikina ciwo yake yi min amma sai na girgiza kaina nace "babu komai, Babu abinda yake damuna" yayi ajiyar zuciya yana kallo na, and once more na saka gain disappointment a fuskar sa, Na sunkuyar da ido na kasa, "Doctor ya baki bedrest amma baki huta din ba ko? You were supposed to be resting 24/7 amma shine kika fita" na da go ido na kalle shi sai na sake mayar wa kasa, ya cigaba "yes, twins sun gaya min kin fita, kika yaudare su cewa gurin dinner zaki je, and you ran away. cewa gurin dinner zaki je, and you ran away daga gurin dinner din suka neme ki suka rasa. The poor kids have been looking all over for you. Ina kika je?" Na cigaba da shiru na "gurin sa kika je ko?" Still shiru. Ya ja kujerar sa baya "ya Rabb. What should I do. What should I do ya Rabbi. Safiyya aure ne akan ki fa yanzu" Mommy ta bude kofa ta shigo, Esther a bayan ta da baskets na abinci. Ta kalle shi ta kalle ni sannan tace "wannan ba lokacin fada bane ba. Wannan yarinyar da kyar aka dawo da ita duniyar mu, she called me Baba Hadiza. Sai kace ta san Baba Hadizan" ya juyo yana kallo na "Baba Hadiza huh? In ita take kiran ki tell her ban gama da ke ba. She took all her kids with her nima ina so ta bar min tawa" ya karasa yana murmushi. Mommy ta fara kokarin hada min abinci shi kuma ya cigaba da magana "Safiya loved them with everything in her. A lokuta da dama har kishi nake yi cewa ni bata damu da ni ba ni da nake da rai kamar yadda ta damu da su su da basu da rai, And I was angry at her when she chose death over life, I thought ta zabi zama da su akan mu ni da ke. I thought she chose to left us because she did not love us enough, Sai da na huce sannan na fahimci gaskiya, she lost everything sanda ta rasa su, she couldn't save either of them, and then she got you and you were her everything, she could save you so she did. I am sure she didn't even. you so she did. I am sure she didn't even had a second thought before she jumped into that water to save you because without you her life would have been meaningless. All their lives would have been meaningless. You are their legacy. You are their dreams" Na rufe idona ina hango fuskokin su a cikin hoton da shine kadai abinda na mallaka na su. Duk da talaucin su but they looked so contented and happy a cikin hoton. Mommy ta ajiye farfesun naman da ta zuba a bowl a gaba na ta fara kokarin tashi na zaune, na tashi ina rike cikina kamar mai kokarin hana dinki na budewa. Ta bini da kallo sannan tayi tsaki "ba kya jin maganar Fiyya. Ji yadda kika koma dan Allah. Skeleton ma ya fiki kyan gani. Ba zan kai ki gidan miji a haka ba wallahi. 16 15 12:56 AM Sai kin dawo hayyacin ki. Kuma ba zaki dawo hayyacin naki ba sai kina cin abinci". Mustapha ya bude kofa ya shigo tare da sallama, Mommy ta juya kansa "daga ina kake? Ka barni ina ta fama ni kadai, kana sane cewa abubuwa sunyi min yawa, ga wadannan marasa lafiyan ga baki a gida ga surukan Safina sunce zasu zo in an jima. Ita tana can ta rufe kanta a daki, Kai ka kama hanya ka yi tafiyar ka yawon ka" yayi shiru yana kallon ta har ta gama sannan yace "Mommy ke fa kika aike ni gidan Hajiya" ta alive flask din hannunta tace "au. haka ne fa. ajiye flask din hannunta tace "au, haka ne fa. Then don't just stand there ka zo ka taimaka masa ya ci abinci". Ya karasa gaban Daddy ya zuba masa kunun da ya gani a flask sannan yace min "sannu" ban kalle shi ba nace "yauwa. Kai ma sannun ka". Mommy ta cigaba da maganganun ta ita kadai, a ciki na fahimci cewa iyayen Muhammad ne suka kira ta zasu zo daukan Safina, ita kuma tace ba zata basu ita ba sai sun zo da Muhammad ya bada hakurin tafiya da yayi ya bar ta a gurin dinner. Sai da Mustapha yazo fita sannan ace min "Hajiya tace tana duba ki. Tace zata zo ta duba ki" na gyada kai kawai. Mommy ta bude ido "da wacce kafar zata z0 duba tan?" Mustapha ta daga kafada "I don't know. Sako ta bani ni dai" ta girgiza kai "zanje gidan in na bar nan. Zan gaya mata cewa likita yace babu dubiya. Ta bari in an sallame ta zata je da kanta ta kaishe ta". Sai a lokacin Daddy ya kalle ta "Sa'adatu, ina zaki je in kin bar nan? Gida gurin surikan Safina ko kuma gidan Hajiya?" Ta zauna tare da yin ajjiyar zuciya "ban sani ba ni kam, Abubuwa sunyi min yawa" yace "ki tafi gida gurin bakin ki, Ki bar hajiya in tazo ma babu komai. Ki basu yarinyar nan su tafi da ita. Kar ki jawo mata rigima a gidan mijinta tun kafin ta shige shi, Mun gode da kulawar ki. We are going to be fine. Zaki iya tafiya ba. We are going to be fine. Zaki iya tafiya ba wani abu" Tun kafin ta tafi twins suka zo, sannan sai doctor yazo ya mayar da Daddy dakinsa yana tsokanar sa wai marar lafiya ya koma dan zaman jinya. Nima kuma ya dawo ya gaya min cewa ba zai sallameni ba tunda banyi hutun da yace min inyi ba. A gida bayan Mommy ta koma bakin nata suka zo. Kannen baban Muhammad ne su biyu da yayyen maman sa suma su biyu, dukkan su mata. Mommy tai musu tarya ta musamman suka gaisa, ta kirawo Safina ma ta zauna daga can ness ta rufe fuska ta gaishe su, sannan suka gabatar da bukatar su ta tafiya da Safina. Daya daga cikin sisters din Mama ta fara magana "Mun fahimci cewa kinyi fushi ne shi yasa kika dauke Safina daga gurin dinner kika taho da ita gida. Kuma a gurin mu fushin ki is justified. Dan haka muka zo da kan mu zamu baki hakuri akan rashin fahimtar da aka samu, muma kan mu lokacin da kuka taho hankalin mu a tashe yake na rashin ganin nasa, mun kuma yi ta kiran wayarsa ba ma samu. Sai da ga baya muka samu ta dan uwansa sai yake gaya mana suna tare, wai ya shigo gurin taron da mota shi kuma angon ya fito yin waya shine ya dan buge shi da motar bai gani ba, Daga nan shine suka tafi a duba kafar ko yaji ciwo, shi yasa muka ji su shiru". Mommy tayi shiru tana kallon su, ta fahimci su kansu da suke fadar maganar ba su yarda da maganar ba. Tace "to ya jikin nasa? Da fatan bai ji ciwo ba" Mammy maman Muhammad Al'ameen tace "da sauki sosai. Bai ji ciwo ba" Mommy tace "Okay tare kuka zo kenan. Yana waje?" Suka yi shiru, sai Mammy tace "ba tare muka zo dashi ba Hajiya. Mu a gain mu idan mu iyayensa muka zo ai mutuntawar tafì ace shine yazo. Muna gain idan muka turo shi muka ce yazo kamar bamu baku muhimmancin da ya kamata ace mun baku ba". Mommy ta gyara zama tace "haka ne. Zuwan naku gaskiya yafi bawa maganar daraja. Amma abinda yasa naso ace yazo saboda ni na kasa gane kan alakar da take tsakanin su da Safina. Ni ban taba ganin aure irin wannan ba. Babu shauki babu fahimtar juna sam a cikin sa. Misali yanzu mu dauka cewa da gaske ne abinda ya gaya muku cewa dan uwansa ya kade shi a mota. A matsayin Safina na amaryar da za'a kai masa a ranar shin bai kyautu ace ya kira ta ya gaya mata ba? Tunda dai ba unconscious aka dauke shi ba. 13 9 g A 12:56 AM Amma maganar da nake yi muku Hajiya tun da muka fito daga gurin taron nan har yanzu bai kira wayar ta ba", Hajiya Hafsat maman Ayaan tace "na fahimci concern dinki Hajiya, duk uwa dole. fahimci concern dinki Hajiya, duk uwa dole ba zata so ace ta kai yarta inda ba'a daraja ta ba, amma in muka yi la'akari da yadda haduwar tasu ta kasance sai muga cewa dama dole ba za'a samu shakuwa a tsakanin su irin yadda muke bukata ba, at least not for now" Mommy ta bita da kallo sannan tace "ban gane yadda haduwa ta kasance a tsakanin su ba? Ta yaya suka hadu din?" Hafsat tace "muma yanzu da muka matsa da bincike akan abinda ya faru din shine mahaifiyar Muhammad take gaya mana. Shi Muhammad mahaifansa sun matsa masa ne suna son ya samo mata suyi masa aure a dalilin wani personal issue, a lokacin ne kuma ita... ." Mammy ta katse ta "ina ganin wannan ba maganar mu bace ba, we only know muma saboda mun matsa sai munji real dalilin fitar sa daga gurin dinner, amma Hajiya Sa'adatu a shawarce kuyi magana da Safina tunda na fahimci cewa baki sani ba, ke ma kuma Safina ki yi magana da mahaifiyar ki, ita ce tafi kowa dacewa da ta baki shawara akan abinda zaki yi. Mu yanzu zamu tafi. Yadda kuka yi sai ki sanar da mu. Amma dai Hajiya ina tuna miki aure dai an riga an daura, igiya uku ce yanzu ta Gidado akan Safina". Suka tashi daya bayan daya suka fita suka bar Mommy a zaune cikin mamaki, ta juyo tana kallon Safina cikin zafin zuciya tace "in kika yi min karya sai na balla ki. A ina kika samo wannan yaron? A yawon banza kuka. samo wannan yaron? A yawon banza kuka hadu ko menene?" Safina ta fara kuka, ta na jin zafin gorin da kaa fara yi mata tun yanzu, yanzu Allah ka dai ya san a dangin Muhammad yawn wadanda suka san cewa ita tacevtana son shi "wallahi Mommy ba haka bane. Kaddara ce ta fada min. Allah ne yayi min jarabawa kuma na fadi. Daga ganin hoton sa Allah ya jarabce ni da son sa. Shine na nemi sister din sa na gaya mata ita kuma ta gaya wa iyayensa, su kuma lokacin suna nema masa mata, shine suka hada mu". Washegari da safe ina asibiti Hajiya tazo duba ni kamar yadda tace zata zo. Nayi wanka kenan na shirya ina cin abinci Mustapha ya shigo da fruit basket a hannun sa yace ga Hajiya nan. Mommy ta dauko min hijab ta miko min "sauri ki sa wannan, wannan kirjin naki da ya cicciko bana son Hajiya ta gani" na karbi hijab din na saka pretending as if Mustapha baiji abinda Mommy tace ba, Ya ajiye basket din ya koma sai gasu sun dawo tare, Lubabatu yarinyar ta tana rike da ita, Na mike tsaye ina murmushi, har zuciya ta ina jina dadin ganin Hajiya, tun da na samu ciki Mommy ta hana ni zuwa gurin ta kuma tun lokacin ban ganta ba. Ta shigo ita ma da murmushi a fuskarta tace "babu ruwa na da ke ai, ni nayi fushi da ke, yarinyar nan ki kira ni a waya ma ba zaki kira ni ba. Sau nawa ina cewa a gaya miki ki kira ni?" Ta fada da fada amma kuma fuskar ta da murmushi, na zauna a kasa a kusa da ita bayan ta zauna. amma kuma fuskar ta da murmushi, na zauna a kasa a kusa da ita bayan ta zauna ita ma nace "bani da lafiya ne Hajiya, kiyi hakuri" tace "gashi nan kuwa ai duk kin rame kin kode sai idanuwa kamar mujiya" ina jin Mustapha yana dariya, ta cigaba '"Aka ce min kuma an daura miki aure. Sa'adatu tana ta fada wai kin ce ba kya son Mustapha ba zaki aure shi ba, ni kuma banga laifin ki ba yarinya, to waye zai auri wannan abu haka kamar lagwani? Kai anya ma kuwa kana cin abinci? Mutum sai tsaho babu kumari makar bushashshen rake? Ni kam ko kyauta aka bani wannan a matsayin miji ba zan karba ba" ya sunkuyo kusa da mu yace "auren ai ba kokawa bane ba Hajiya. Kuma kiba ko rashin ta bashi ne yake nuna mazantaka ba". Hajiya ta rafka salati, yayi sauri ya mike yayi waje, Mommy ta juyo da sauri "me yace? Me yayi?" Hajiya ta maimaita mata abinda yace, Mommy ta zauna akan gado "ya Rasulullah ka kawo min agaji, wadannan yaran suna so su kaini lahira" ni dai bance komai ba dan ni Mustaphan da na sani zai fadi abinda yafi wannan nauyi ma, Hajiya ta jima tare da ni. A lokacin naji suna maganar Safina da Mommy, na kuma fahimci Safina still tana gida Mommy tace bata gama yanke shawara akan ta ba tukunna. Washegari doctor yace zai sallame mu ni da Daddy gabaki daya, amma still yace in cigaba da kwanciya ina hutawa kuma ina cin abinci sosai. Kafin ya rubuta mana sallamar ne was bakin suka sake zuwa dubani. Umma, mahaifiyar Mukhtar, tare da kanwarsa Salima. Mustapha ne ya shigo da su. Suma lokacin sun tarar da Mommy a guri na. Suka zazzauna akan kujerun da suke dakin suka gaisa da Mommy, sai dai kallo daya nayi wa fuskar Umma naji gaba na ya fadi. Wannan ba fuskar umman da na sani bace ba, umman da kusan ita ce third mother dina dan daga Mommy a guri na sai ita, tunda Aunty Hajjo ba haduwa muke yi ba sai muyi shekaru ba mu ga juna ba. Na sauko daga kan gadon da nake na durkusa har kasa na gaishe ta, tayi min irin amsawar da ni da nake kusa da ita ma banji ba ballantana sauran mutanen da suke dakin. Mommy tayi murmushi "Fiyya tana gaishe ki baki ji ta ba maman Salim" ta juyo tana kallona tace "naji ta mana, na amsa mata ma, ko baki ji na masa miki ba?" Ta tambaye ni, ban bata amsa ba sai na sunkuyar da kaina kawai ina jin kamar zanyi kuka. Salima ta yi min sannu na juya gurin ta na amsa muka gaisa, sai ga Mukhtar ya shigo, hannayensa rike da ledoji manya, ya zo ya ajiye su a gaban Umma sannan ya gaishe da Mommy, ta dauke masa kai itama ta amsa masa a ciki, sai yace da Umma "yanzu Abba yake gaya min kun taho nan. "yanzu Abba yake gaya min kun taho nan shine na biyo bayan ku, sai na ga kun manta wannan sakon a mota shine na shigo muku da shi" ta harare shi sannan tayi tsaki tace "ni ban manta komai ba, babu abinda nazo da shi. Kai dai kawai tunda ka siyo kayan ka zaka kawo mata shikenan sai ka bata ai matar ka ce babu mai hana ka, amma kar ka saka ni a ciki. Rasa kunya beran salga". Sai kuma ta mike "to Allah ya bada lafiya" Mommy tace "Amen, mun gode" ta fita Salima tana binta a baya, Mukhtar ya cigaba da zama, da ga alama ya dauka Mommy zata je ta raka ta hanya, ganin bata da niyyar tashi sai ya mike shima. "Ina wayarki?" Ya tambaye ni, ban kalle shi ba na bude hannayena alamar oho, ni na manta ma ina da waya. Ya dan daga murya yace "ban san baki da lafiya ba, babu wanda ya gaya min baki da lafiya, and I should be the first to know, I should be the one to stay here with you" fahimtar cewa rigima yake son tayarwa sai na dago kaina nace masa "in an jima za'a sallame ni. Na warke already. Kaje ka raka su Umma" kamar ba zai fita ba kuma sai ya fita din. Yana fita Mommy tabi bayansa da harara, sannan tace "waccan matar ta san maganar nan. Kin ga abinda kika jawo wa kan ki ko Fiyya, kin fara gani ko? To wannan somin tabi ne, ita wannan yanzu ita kika zaba a matsayin surikar ki, ita zata zama kakar yayan ki" ban ce komai ba ina ta jujjuya hannu na. hannu na. Sai kuma cewa tayi "shegiyar mata mai kama da muciya" Mustapha ya fara dariya sai ta nuna masa hanyar waje "fita ka bani guri, marar kunya fitsararre". Na dauka Mukhtar zai dawo suyi rigima da Mustapha amma bai dawo ba, daga alama yabi su Umma sun wuce. Har aka zo aka bani takardar sallama, dama already an kwashe duk kayan mu an tafi dasu gida, Mommy ta tafi gurin Daddy ni kuma ina hada abubuwan da suka rage mana sai da Mustapha ya shigo dakin da nake. Na juyo ina kallon sa shima yana tsaye a bakin kofa yana kallona sai nace "bata nan, ta fita" ya karasa shigowa tare da rufe kofa ya murda key din jiki. Nayi baya da sauri ina neman nearest makamin da zan iya kare kaina da shi. Idanuna suka sauka akan yar karamar wukar da aka yanka fruits da ita dazu, na dauka da sauri na nuna shi da ita. "get out!" Na fada sternly, "ka fita ko in cika alkawarin da na daukar maka, the next time you put your filthy hands on me will be the last time you ever have hands" ya jingina da jikin kofar tare da saka hannayensa a cikin aljihu "na sani, I remember exactly what you said. And I promise you that I will never touch you again. Magana kawai nazo muyi" Na cigaba da nuna shi da wukar ina jin zuciya ta a bushe "I don't want to talk to you har sai na samu evidence. Now get out tun. dazu, na dauka da sauri na nuna shi da ita. "get out!" Na fada sternly, "ka fita ko in cika alkawarin da na daukar maka, the next time you put your filthy hands on me will be the last time you ever have hands" ya jingina da jikin kofar tare da saka hannayensa a cikin aljihu "na sani. I remember exactly what you said. And I promise you that I will never touch you again. Magana kawai nazo muyi". Na cigaba da nuna shi da wukar ina jin zuciya ta a bushe "I don't want to talk to you har sai na samu evidence. Now get out tun kafin in haka ramuka a jikin ka da wannan wukar". EPISODE TWENTY THREE owner 16 6 8:49 PM Safiyya Episode Twenty Three: Unexpected Paid Advert *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*, *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332*. Ya cigaba da tsaiwa a gurin yana kallona kamar baiji abinda nace ba, zuciya ta fara tafasa, he doesn't believe that I can do anything to him, na fara takawa zuwa inda yake still da wukar a hannuna "| mean it! Ka fita ko kuma a fitar da gawarka" ya daga hannu "okay, okay, zan fita. But still ina so muyi magana, maybe inkin kara hucewa. God knows I have been trying my best inga mun shirya kin ki. I have made a mistake amma na san babu wanda yake above mistake. Har ke ma" ya karasa maganar yana murmushi sannan ya murda key din kofar ya bude, har zai fita kuma sai ya juyo yana kallona yace "at least ni nawa mistake din bai fito duniya ta ganshi ba, naki kuma rai ne da shi ma, staying there for all to see" yayi sauri ya karasa fita ya rufe kofar. Na jefar da wukar sannan na zauna a bakin gado ina kallon bangon dakin blindly, only god knows how much na tsani Mustapha maybe shi yasa bai kaddara zai zama mijina ba dan da ya zama da tabbas za'a iya rasa daya daga cikin mu. Amma kuma yanzu concern dina ba akan Mustapha bane ba tunda issue din auren sa ya riga ya wuce, yanzu akan mukhtar ne, mukhtar din da na zaba da kaina a matsayin miji, I do not love him but I respected him, sai dai now after what happened ranar nan da daddare, da yawa daga cikin respect din da nake bashi ya gushe daga zuciyata, But then mijina ne, it wasn't wrong for him to try kissing me islamically, but his timing was emotionally wrong. Sai dai kamar yadda mommy ta fada, ni na. Sai dai kamar yadda mommy ta fada, ni na zabi kayana and now I have to live with the consequences of my decision. Ina nan a zaune mommy ta shigo tace an fita da daddy in taso mu tafi. Na mike na dauki yar karamar jakar da take gabana na fita. Kwana biyun da nayi a asibitin naji dadin jikina sosai, na dan samu karfi a jikina kuma na huta sosai. Ina fita naga mukhtar yana tahowa inda muke, mommy tayi tsaki "wannan yaron ko maye ne sai haka" yazo ya karbi jakar hannuna "you shouldn't be lifting abu mai nauyi, na tabbatar sun gaya miki haka" nace "babu nauyi ai" ya rataya jakar a kafadar sa daya sannan ya rike hannuna da daya hannun, na zame hannuna da sauri "I am fine" ya tsare ni da ido "ban yarda ba, in kika fadi kuma fa? If it was up to me I will carry you to the car" na yi sauri na zagaye shi na koma side din mommy wadda na tabbatar taji abinda yace sai dai bata ce komai ba. Muna zuwa naga Mustapha yana taimakawa daddy wajen shiga mota, na karasa gurin na bari sai da ya zauna sosai sannan na gaishe shi nayi masa sannu. Yana kallo na yace "how are you feeling?" nace "na warke, naji sauki sosai" ya gyada kai "good. That's good, Shiga mu tafi", Mukhtar ya matso ya gaishe shi shima sannan yace "zamu tafi tare da safiyya a mota ta tunda naga kuna da yawa anan din" na juya ina kallon yawan namu, Mustapha ne kuma shi zai yi driving, sai mommy sai ni sai twins amma kuma twins da mota suka zo. Nayi sauri nace "it is okay. Twins da mota suka zo ai, It is just me. okay. Twins da mota suka zo ai. It is just me and mommy" mukhtar ya tsaya yana kallona bai ce komai ba, daddy yace "ku je, zamu hadu a gida" har mukhtar ya juya sai kuma ya kira sunan sa, ya juyo sai yace masa '"bata da lafiya, kar ka kaita wani guri. Gida zaka kaita direct daga nan. I mean it" bai jira amsar mukhtar ba yaja kofa ya rufe. Mommy ta fara magana "sabon iyayi, ai kuma shikenan mun shiga ukun mu..... " ban ji karshen maganar tata ba saboda shiga da tayi cikin mota ta rufe kofa amma nasan har zuje gida ba zata yi shiru ba. Nayi ajiyar zuciya bayan sun ja motar feeling alone and vulnerable har sai da suka fita daga building din sannan naga tsayuwar motar yaya mukhtar a gaba na. 14 10 8:56 PM ya bude kofar motar yace "get in" na shiga na zauna na rufe muka fara tafiya, ban san me yasa ba kawai sai naji na takura, ba wai anar ne na fara shiga motar mukhtar ba dan gfarkon zuwana Abuja kafin uncle ahmad ya yarda a bani mota mukhtar shine ya zama kamar driver na to and from school, zuwa shopping, zuwa duk was unnecessary yawo na duk inda nace zanje to zai ajiye duk abinda yake yi ya kaini, "hey" naji muryarsa ta katse min tunanina, "tunanin me kike yi ne haka?" na juyo na kale shi sai yayi min murmushi, na sunkuyar da kaina ina jin kamar wadda take yin abu ba dai dai ba, somehow tafiyar da muke yi yanzu tare da shi a mota reminded me so much of Muhammad and mv heart feels. much of Muhammad and my heart feels kamar ina cheating on Muhammad din ne. na gyara zamana ban ce komai ba sai yace "just tell me tunani na kike yi shikenan" sai na samu kaina da murmushi, only if he knows tunanin wanda nake yi. Ya cigaba "bana son wannan shirun da kika koya kwanan nan, the fiyya I know would have break my ear drum da surutu yanzu. Na sake yin murmushi ina tuno waccan fiyyan, na girgiza kaina "she is gone. That fiyya is gone. Yanzu wata ce sabuwa, and you have to get use of this sabuwar" yayi ajjiyar zuciya "yeah, may be. Maybe kuma I will have to work on bringing her back to life" na juyo in kallon sa nace "anya kuwa? Ka taba ganin wanda ya mutu ya dawo?" yace "wanda ya mutu baya dawowa safiyya amma ni a yanzu idan da darasin da rayuwa ta koya min a shine nothing is impossible, babu wani abunda mutum zai iya cewa ba zai iya achieving ba a rayuwa. You just have to work hard ka kuma yi ta addua. Ban taba tunanin akwai ranar da zan kira ki matata ba, and today you are my wife. Na juyar da kaina ina kallon motocin da suke wucewa. Ita kaddara most of the times is a complicated something, ba zaka taba gane yadda take working ba sai ta saukar maka tukunna, All the small pieces of every event na rayuwar mu, all the small decisions and choices da muke making a rayuwa, they all work together and shape our kaddara, and addua glued them together, Yay gyaran murya na juyo ina kallonsa sai ya sake yi min murmushi. "na ga alamar wannan tunanin ba. murmushi. "na ga alamar wanna tunanin ba zai barki ba, and I really want to talk to you. Ina son in baki hakuri about the other day. Naga ranki ya baci sosai and I know I shouldn't have done what I did. But you are my wife ko? So babu laifi ai ko?" Still ban bashi amsa ba sai najimya tsayar da motar, na juyo da sauri ina kallonsa sai yace "safiyya you have to say something. Ba zai yiwu inyi ta magana da kaina ba kamar radio, na san ni na ce ina sonki ni kuma nayi ta naci akan hakan, amma ke kika amince da kanki kika ce zaki aure ni then it is not a forced marriage Kenan. Ina saka ran for you to chose me then at least there is an ounce of my love in your heart. Dole kuma sai kin bani dama sannan zan gina masarautata a zuciyarki" na kale shi cikin ido nace "banajin dadi ne yaya mukhtar, zuciyata, jikina da tunani na gabaki daya basa cikin hayyacin su a yanzu. I have made a lot of bad decisions because of halin da na samu kaina a ciki. Some of them have caused me a lot. Please kar ka zama one of those decisions. need you to be the strength that I lack, I need you to help me pass through wannan storm din da nake ciki. This is not the right time to discuss love and marriage, A time will come for that" Ya juyo sosai yana kallona ya kama hannuna ya rike, "I will be whatever you want me to be. In akwai abinda yake damunki tell me, in akwai wanda ya takura miki tell me inyi miki maganinsa. I just need you to involve me a cikin duk abinda yake faruwa a rayuwarki, but for that I need you to talk to me" na. but for that I need you to talk to me" na cigaba da kallon fuskarsa, trying to study it, sai na samu kaina da rashin son abinda na gani a idonsa, I have seen something similar a lokuta da dama and I do not like it. Na zare hannuna daga cikin nasa tare da sake juya fuskata gefe. 15 8:56 PM Yayi ajiyar zuciya "and how do you want me to be all what you mentioned when you always withdraw from me" na juyo ina kallonsa nace "what do you want to know? Wacce maganar kake so inyi maka?" yayi shiru yana tunani sai kuma yace "anything, especially personal things wadanda zasuyi creating bond a tsakanin mu. For example let's talk about your CS, how did it go? Where is the baby? Daga ke har daddy babu wanda yake magana akan what happened a Berling". Nace "the CS went fine, anyi shi early ba a date din da aka saka ba saboda na fara rashin lafiya. The baby is fine, yana can a NICU dinsu because he is preterm" ya saka motar a gear muka cigaba da tafiya sai yace "namiji ne kenan?" ban kalle shi ba nace eh. Ya cigaba da tafiya "what do you intend to do with him?" nace "I don't know, I am not sure" ya danyi shiru sannan yace "We can raise him together" na girgiza kaina "not an option. That will expose him to the world. Mutane sun san sanda aka yi mana aure kuma sun san bamu haife shi ba" ya cigaba da driving "ya maganar barin Nigeria da kika. da driving "ya maganar barin Nigeria da kika taba yi min? ina ganin hakan idea ce mai kyau, we can move out mu dauke shi and settled somewhere" na juya ina kallon shi bance komai ba, sai ya cigaba "that way za ki fi healing, away from all that hurt you, away from wadancan mayaudaran guda biyu" na rufe ido na ina jin kaina yana fara yi min ciwo" ya cigaba "any news a kan su? Da akwai abinda safina ta gaya miki ne ranar nan?" na bude idona "please yaya mukhtar ka daina yi min maganar su. I do not want to talk about them. Please, just take me home". Daga nan sai yayi shiru din kuwa and we drove in silence har muka je gida, na san cewa su daddy already sun je gida by then saboda tsayawar da mukayi a hanya ga kuma dama Mustapha shegen gudu ne da shi a mota. Muna zuwa mai gadi ya bude mana gate muka shiga, idona yana rufe ina sauraron yadda kai na yake sarawa. Sai naji mukhtar yace "woaw!" yana yin yadda yayi maganar ya saka na bude idona da sauri na kale shi snnan na kalli inda yake kallo, and then I saw him, Muhammad ne a tsaye a compound din gidan mu a jingine da jikin sabuwar lexus dinsa, hannayensa cikin aljihunsa, idanuwansa akan motata da take ajiye a gefe, Naji numfashi na ya tsaya a wuyana, Muhammad a cikin gidan mu? Something that I have pictured and hoped for years amma yanzu gashi a gabana amma in an indescribable way. Mukhtar ya taka burki yana kallona yace "shall we go back?" ban. yana kallona yace "shall we go back?" ban bashi amsa ba Muhammad ya juyo ya sauke idanunsa akan mu. Na lura da yadda ya gyara tsayuwarsa ya mike straight and his eyes darted from me to mukhtar and then back to me. Mukhtar ya karasa shiga da motar muka wuce ta gaban gidado sannan yayi packing, ya juyo yana kallona yayin da ni kuma na rufe nawa idanun. "do you want us to go back?" ya sake tambaya. Na harhado courage dina guri daya nace "what for? In mun koma hakan zai dawo min da rayuwata one year back? Hakan zai dawo min da duk abubuwan da na rasa" bai amsa min ba sai kuma ya tambaya "me yake yi a gidan nan? Me yazo yi?" na bude ido na nace "yazo bawa matarsa hakuri kuma ya dauke ta su tafi" na fadi maganar da baki na amma zafin ta yana tafasa zuciyata. Mun jima zaune a cikin mota babu wanda ya sake yin magana. Bana ganin Muhammad daga inda nake amma zuciyata tana gaya min cewa motar yake kallo har yanzu. And here I am sitting in the car with my husband. Na daga hannuna na kama handle din kofar sai na ji ta a rufe, na juya na kalli mukhtar sai yace min "don't, kar ki manta nima ina da zuciya a kirjina, You will neither see him nor talk to him, ever" ya fadi kalmomin daki daki with a very serious tune. Na tsaya ina kallonsa, and he looked dead serious, Na juya da sauri ko zan sake ganinsa sai mukhtar ya saka motar a gear ya fincike ta a reverse a guje ya sake fitar damu daga. reverse a guje ya sake fitar damu daga gidan. As we were going out of the house, I saw Muhammad moved from inda yake a tsaye kamar zai biyo bayan mu but he didn't. Him 11 11 安1 8:56 PM Ranar da ya bar gurin dinner a gidan Ya Amen ya kwana, tun da suka je gidan wayarsa ta fara kara dan haka ya kashe ta dan akwai wadanda zasu kira shi kuma ba zai iya kin dauka ba. Shi ya san yadda yake jin zuciyarsa a lokacin, ya tabbatar da maganar Al'ameen cewa rashin zamansa a gurin ya fi zaman na sa alkhairi dan ba karamar kura zai tayar da idan ya shiga. He blamed everyone for what happened, including Ya Amen dan har da shi akayi ta convincing dinsa cewa he was being delusional sanda yake tunanin cewa Safina is related to Safiyya. Sai da Al'ameen ya bashi hakuri sannan ya daina blaming dinsa, ya koma blaming wadda yake ganin gabaki daya laifin nata ne, Safina. He called her a liar and a pretender more times than he count a cikin dare daya, Ya samu some of his answers, duk da dai cewa most of the answers shi yayi concluding kayansa, but the answers also raised some more questions, Idan har da gaske Safina step sister din Safiyya ce then waye Alhaji Adam Muhammad? Baban Safiyya ko mijinta? Idan babanta ne da aaske to wave milin nata? And is she trulv. gaske to waye mijin nata? And is she truly married or not? Ina cikin jikinta yake? And the most important question, what happened to her da ya mayar da ita yadda take yanzu? Al'ameen got the worst of Gidado a daren nan, he channelled all his anger and questions toward Al'ameen, tun yana kokarin trying to help him figure out wadansu answers din har ya koma yayi tagumi ya zuba masa ido. Shi yasan soyayya, dan haka zai iya kwatanta abinda Gidado yake ji a ransa. Daga baya masu kiran wayar Gidado suka koma kiran ta Al'ameen, daga dukkan alama sun fahimci shima baya gurin. A dole ya dauka bayan inda inda da rashin sanin abinda zai ce musu sai ya gaya musu cewa ai shine ya buge Gidado da mota kuma ya tafi da shi asibiti. Daga shi har wadda ya gaya wa sun san cewa karya yake yi, wannan ya saka suka cigaba da tambayar sa gaskiya a karshe dai Maman Gidado ta karba ta tambaye shi a wanne gidan suke ya gaya mata suna gidan sa sai kawai ta kashe wayar. Ta san Gidado ba son auren yake yi ba but she thought ya karba tunda har ya bari aka daura, she never expects him to retreat back ana tsakiya da biki, Ranta ya baci akan hakan musamman da Mommy tayi kokarin tayar da hayaniya a gurin tare da dauke yarta, but she kept her stance har aka gama taro aka sallami baki, amma tayi alkawarin. taro aka salami baki, amma tayi alkawarin bata wa Gidado ransa dan suka koma gida. Sai dai bayan an tashi daga taron ma bai koma gidan ba, but he kept asking Al'ameen ya kira yaji idan an kai amarya, daga baya dai da suka yi bincike suka gano abinda ya faru, amarya dai ba'a kaita ba, Mommy ta mayar da ita gida kuma tace sai yaje ya bada hakuri sannan zata bashi amarya. He smiled, shook his head and said "zata rube a gidan kuwa". But he wants her to come. Yana so su kasance shi da ita because daga bakin ta ne zai samu dukkan amsoshin tambayoyin sa, a yanzu ita ce link dinsa da Safiyya, link din da ya jima yana kokarin establishing. Sai dai zuwa yanzu ya riga yayi tagging dinta a matsayin makaryaciya, dan haka dole zai bi a hankali wajen gain ya samu gaskiyar magana daga bakinta. Washegari yaje gida, all set and ready for fadan da yake jiransa, a kuwa ya samu fadan dai dai gwargwado dan Mama bata yi masa da sauki ba, Shi ya san babban abinda zai kara triggering Mama a lokacin shine idan ya fada mata cewa Safiyya ya gani a gurin dinner, that Safiyya yar uwar Safina ce, ya san idan ya fadi haka Mama sai ta tsinewa dukkan generation din Safiyya, baya jin akwai abinda Mama ta tsana a yanzu sama da sunan Safiyya ba ma ita kanta ba, Sai da ya gama karbar fadan sa, ya samu. Sai da ya gama karbar fadan sa, ya samu auntie dinsa suka bada hakuri, sannan Mama tayi musu bayanin dalilin da ita take ganin ya saka shi ya bar gurin dinner, that his mind is on some "shegiyar yarinya" da ta shanye ruhinsa and that he doesn't love his bride. 9 8:56 PM Yaji dadin da aunties din nasa suma tausaya wa lamarin sa, wasu daga cikin su har suka yi arguing cewa hukuncin da aka yanke nayi masa aure ba dai dai bane ba, sannan kuma suma yi volunteering cewa zasu je su bayar da hakurin on his behalf. He thought that zasu taho masa da Safina and he will get his answers that day, sai dai haka suka dawo hannu rabbana, but da alkawarin cewa maman Safina zata kira da kanta ko kuma ta kawo yar tata da kanta. Sai dai har aka kwana biyu bata kira din ba kuma bata kawo ta din ba. And he couldn't wait any longer. Tun a kwana na farko yaje gidan Hajiya, tunda can ne inda ya sani, sai dai bai bar mutanen gidan sun san yazo ba he asked maaikatan gidan inda Safina take and he got the address na gidan da aka ce anan ne Safinar take a wannan lokacin "gidan marikin ta ne, mijin mahaifiyarta, a gurin sa ta girma ai dan haka can ne gidan su" mai gadin nan mai surutu ya gaya masa, Ya rubuta address din a goggle map dinsa sannan ya sake tambaya "shine Alhaji Adam?" Yayi shiru yana jin zuciyarsa tana buaawa, waitina for the answer, mai aadin. Adam?" Yayi shiru yana jin zuciyarsa tana bugawa, waiting for the answer, mai gadin yace "eh Alhaji Adamu ba. Mutumin kirki ne ai sosai. Ya rufe ido yana jin wani abu yana sauka a cikin zuciyarsa. So Safiyya didn't lie about her father, she is not a gold digger. Babanta ne Daddy ba wai mijinta ba. But how comes aka saka sunan ta a matsayin matarsa? Yayi tunanin sake using wani card din ko zai kuma samun amsa amma kuma baya son tsohon mai gadin ya zarge shi da wani abu. "okay, okay na gane Alhaji Adamu, shine baban Safiyya ko?" To his delight sai mai gadin ya gyada kansa "eh shine. Yarinyar kirki. Ai bata da lafiya ma. Yanzu Hajiya ta tafi duba ta" Gidado ya bude ido yana jin zuciyarsa tana bugawa "me ya same ta?" Mai gadin ya daga kafada "ban sani ba, bata dai da lafiya. Hajiya naji tana fada". Gidado ya saka motarsa a reverse da sauri sai kuma ya dakata ya dauko kudi a aljihunsa ya mika wa mai gadin, sannan ya bar kofar gidan a guje ya doshi kwatancen da aka bashi, Shi kansa bai san in yaje gidan me zaiyi ba. Zai ce yazo bawa safina hakuri ne kamar yadda mahaifiyar ta ta nema ko kuma zai ui pretending as if yazo duba Safiyya ne. But that will sound odd considering the. that will sound odd considering the situation. Har yaje gidan bai yanke shawarar abinda zaiyi ba. Sai dai tun daga gate mai gadi ya hana shi shiga ya kuma gaya masa cewa masu gidan basa nan. "Alhaji ba lafiya, duk suna asibiti gabaki daya" yayi shiru yana tunani, Safiyya aka ce masa bata da lafiya ba Daddy ba, ko dai ba gidan yazo ba? Ya sake tambaya "Safiyya ma bata nan?" And the rude mai gadi just said "eh bata nan" and closed the gate. Muhammad ya tsaya yana kallon gate din da sakakken baki. No, this mai gadi will not stop him from getting inside. Ya bude kofar motar ya fita yayi knocking a gate din, mai gadin ya sake budewa ya tsaya yana kallon sa, irin kallon tuhumar nan, Muhammad yace "sunana Muhammad, nine mijin Safina ta gidan nan, na san baka sanni ba" sai yaga mai gadin yayi murmushi "angon ne ai ashe. To ai ni ban sanka ba. Bismillah bara a bude maka kofa. Ai farko Safiyya kace shi yasa kaga na ki kulaka saboda doka ce daga Alhaji kar mu bar wani wanda bamu sani ba yazo gurin Fiyya" Muhammad ya kirkiri murmushi, a zuciyarsa yana adding question din why a cikin jerin questions din da yake da su. Amma a fili sai yace "naji ance bata da lafiya ne Safiyya, shi yasa kaji na tambaye ka ita" mai gadi yace "eh bata da lafiya, ita ma duk suna asibiti, Su Hajiyan ma duk suna tare da su a can. Hajiya Safina ce dai ban tabbatar ko tana ciki ko kuma tana asibitin ba, ko a. ko tana ciki ko kuma tana asibitin ba, ko a dubo maka ita?" Muhammad ya girgiza kai "no. Zan kira ta a waya. shikenan, na gode" Ya juya ya koma cikin motar wanting with all that is in him ya koma ya tambayi wanne asibitin ne amma kuma bai san me zaiyi a asibitin in yaje ba. Ya zauna ya kwantar da kansa akan head rest din motar yana bitar amsoshin da ya samu so far. Da kuma sabbin tambayoyin da amsoshin suka yi creating. Zuciyar sa tana kwadaita masa "she is not married. 10 9 8:56 PM Karya tayi maka" but why will she lie? Idan kuma da gaske kara tayi masa then da gaske bata son sa ne tana so ne ta rabu da shi, idan kuma haka gaskiya ne then all this is for nothing. Gidan Al'ameen ya koma dan har yanzu Mama da Abba basu huce da shi ba, a can ya sake kwana sannan washegari ya yanke shawarar komawa neman labarin Safiyya in the guise of neman Safina. Ranar yana zuwa mai gadi ya gane shi ya bude masa gate ya shiga, Muhammad yayi packing yana kallon tangamemen gidan da yake gabansa, gidan su Safiyya, gidan da ya roki Safiyya ta kawo shi sau ba adadi tana kawo masa excuses, But the house looks empty kamar ba'a zama a cikin sa sosai. Mai gadi ya zo har inda yake ya gaishe shi ya kuma dava masa cewa Safina tana ciki dan. gadi ya zo har inda yake ya gaishe shi ya kuma gaya masa cewa Safina tana ciki dan ya ga shigar ta dazu, sannan kuma ya kara da cewa "yan asibitin ma an sallamo su sun dawo, yanzu aka shiga da Alhaji ciki" ya hadiye abinda ya tsaya masa a zuciya yace "har Safiyya?" Mai gadin yace "a'a ban ga shigar Fiyya ba. Maybe ba'a sallamo ta ba ita" Sai kuma ya wuce ciki yana cewa "bara in sanar musu cewa kazo" an jima kadan ya dawo zai bashi amsa sai kuma ya jiyo horn a gate, dan haka ya wuce da sauri bakin gate din. A lokacin ne Muhammad ya ga motar Safiyya, ya tsaya yana kallon ta, so it really is true, duk wadannan abubuwan da yake ganin su kamar a mafarki da gaske ne ashe, Da gaske gidan su Safiyya ya shigo yau yake tsaye a cikin sa but a matsayin mijin Safina. And then he felt that feeling, and he knows cewa ta shigo gurin. Ya juyo suka hada ido. Ita din ce a zaune a mota da cousin dinta Mukhtar a gefen ta, that Mukhtar that he doesn't like, Suka wuce shi and packed a bayan sa. Ya tsaya yana kallon motar yana jiran yaga abinda zai faru, many questions running through his mind, Why are they together? And me suke yi a motar da ba zasu fito ba? And his whole world came crashing on him. Wani irin kishi yaji yana kona zuciyarsa, so yake yi kawai yaje ya finciko Mukhtar daga cikin motar yayi ta dukan sa ba dan yayi masa komai ba. Ya fara tafiya toward da car kenan sai Mukhtar din. jiran yaga abinda zai far, many questions running through his mind. Why are they together? And me suke yi a motar da ba zasu fito ba? And his whole world came crashing on him. Wani irin kishi yaji yana kona zuciyarsa, so yake yi kawai yaje ya finciko Mukhtar daga cikin motar yayi ta dukan sa ba dan yayi masa komai ba. Ya fara tafiya toward da car kenan sai Mukhtar din yayi reverse da motar a guje ya fita daga gidan kamar yadda ya shigo. Episode Twenty Four owner 5 8:39 PM Safiyya el LTE 0 Episode Twenty Four: The Interview *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad.* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*. *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332*, Yabi motar da kallo, contemplating on what to do, his first thought was to follow them, but why will he do that. As far as he knows Safiyya matar aure ce and that guy da suke. Safiyya matar aure ce and that guy da suke cikin mota tare is her first cousin, shi kuma matsayin sa shine mijin step sister din ta. In ya bisu mai zai yi musu, menene business dinsa da su? But zafin da yake ji a zuciyarsa kept increasing ta yadda har idanunsa sai da suka yi ja, ji yake kamar kansa yana turiri. Shin haka zafin kishi yake? Shin haka shi tasa kaddarar take? Shin haka rayuwar zata cigaba ko akwai ranar da zai daina jin wannan zafin a zuciyarsa. Shin akwai light at the end of the tunnel? Mai gadi ne ya dawo daga rufe gate din da yayi ya cigaba da kokarin yi masa magana "yallabai ance ka shigo, bismillah" Gidado ya kalle shi kamar lokacin ya fara ganinsa, sannan ya kalli gate din kamar mai neman ta inda Safiyya zata tsaga gate din ta shigo. Sai ya girgiza kansa, not now, not like this, ba zai iya shiga cikin gidan ba a yanzu, he is not functioning right kuma baya so yayi messing up position dinsa a yanzu. Ya juya yana kallon mai gadin yace "tell them an kira ni emergency yanzu, wani uzuri ya taso min na fita" ba tare da ya jira amsar mai gadin ba ya shiga motar sa da sauri ya kunna ta, he used all his self control to keep calm har ya fita da motar daga gidan and then he lost it ya ci taya a waje ya figa a guje, without knowing where he would go. The first thought that came to his mind was 'irin wannan yanayin shi yake saka mutane da yawa shaye shaye ko' and then 'what will. 'irin wannan yanayin shi yake saka mutane da yawa shaye shaye ko' and then 'what will it feel like to get something that will take away all his pains ya dan samu zuciyar sa ta huta' yayi sauri ya kawar da tunanin daga zuriyar sa tare da karanto dukkan adduoin da ya sani na korar shaidan dan yasan sharrin sane, shi yake kokarin saka masa wanna mugun zaren. But then he thought that seriously dole ya nemi wani abu da zai ke dauke masa hankali daga wanna pain din da yake ji a zuciyarsa kafin yayi figuring it out, or maybe kafin pain din ya tafi. And the thought of going to the gym came to his mind. Ya taba jin cewa gyming relieve stress and makes the mind more focus, kuma shi babban abinda yake nema a wannan lokacin shine focus din. Wani friend dinsa ya kira that is into gym, ya tambaye shi ina ne best gym a garin Abuja shi kuma ya lissafa masa guraren da ya sani masu kyau da kuma addresses dinsu. Ranar Al'ameen bai koma gida ba sai da aka fara kiran sallar isha, ranar ko sallar magrib din da suke yi kullum tare da Abba bai je sunyi din ba. Sai daya gama zagaye gyms din nan kaf ya kuma samu wanda yayi masa sannan yayi register da su. Yana shiga gida abinda ya fara lura dashi a compound din shine bakuwar motar da bai sani ba, amma kuma bai damu ba dan har lokacin baki basu gama tafiya ba, wasu ma wadanda basu samu zuwa bikin ba a lokacin. wadanda basu samu zuwa bikin ba a lokacin suke zuwa suyi murna da fatan alkhairi su tafi. Dan haka kansa daya ya shiga cikin gidan ba tare da tunanin komai ba. Amma sai dai yana bude palon Umma suka yi ido hudu da Mommy, a kusa da ita a zaune a kasa Safina, fuskarta a rufe da mayafin ta irin yadda amare suke yi ranar da za'a kai su gidan miji. Yaji kamar ya juya da baya ya koma inda ya fito, amma kuma ba zai iya yin hakan ba dan kusan duk wadanda suke zaune a falon sun ganshi. Ya karasa shigowa a hankali yana lura da kallon da kusan kowa a falon yake yi masa. Mommy tana yi masa kallon "dan rainin hankali" Umma tanayi masa kallon "ka bani mamaki Muhammad" Abba yana yi masa kallon "zaka hadu da ni ne, I will deal with you". 18 14 8:42 PM Ya fara tunanin wanda zai fara gaisarwa a cikin su, sai dai tun kafin ya yanke shawara Abba yace "daga ina kake? Ina wayarka?" Ya fara shafa aljihunsa, shi kansa bai san inda wayar take ba, maybe a mota maybe kuma ya yar da ita in one of the places he has been to, Yanzu shi baya bawa waya muhimmanci saboda rike ta a hannu yana hana shi natsuwa, in dai zai dauki waya sai ya tuna da Safiyya, Babu abinda yake so irin ya ga ya kira ta ta dauka sun sha hirar su irin yadda suka saba. Hausawa sunce sabo turken wawa. turken wawa. "Uhm... I don't know Abba. Maybe in the car", "Zauna!" Abba ya fada almost cikin fushi. Muhammad ya zauna a tsakiya yana jin shi kamar a gaban jury, sai dai bai san hukuncin da za'a yanke masa ba. Abba ya cigaba da magana "ya muka yi da kai kafin a daura auren nan? Mai kace da ni da bakin ka?" Yayi shiru, Abba ya sake maimaita wa "mai kace min sanda na tambaye ka for the final time akan amincewar ka" Muhammad ya dago kai yana kallon sa yace "cewa nayi na amince Abba" Abba yace "okay and then daga baya sai ka fasa amincewar? A haka zaka girma kana yin magana biyu? Haka kaga muna yi?" Muhammad ya girgiza kansa "Abba ba cewa nayi na fasa ba, dazu ma ai naje gidan nasu.. ." Mommy tace "kaje, ance ka shigo sai kuma ka sake chanja shawara ka shiga mota ka fita". Ya sunkuyar da kansa bai ce komai ba. Mama tace "Muhammad ka bani mamaki Allah. Mu dai mun yanke hukuncin mu mun gama. Yanzu kuma mun danka hukunci a hannun ka, Sai muga iya kacin hankalin ka. Sai muga idan kai mutumin kirki ne ko akasin haka. Ga Safina nan an riga an daura auren ku da ita. Ya rage naka ka rike amanar ta kamar yadda iyayenta da mu muka danka maka, ya kuma rage naka kaci amanar ta ka hadu da fushin Ubangiji. Tunda dai da amincewar ka aka yi komai. Sannan dai dai gwargwado munyi iyakacin kokarin mu na ganin mun baka ilimi na zaman duniya da. ganin mun baka ilimi na zaman duniya da lahira". Ta juya gurin Mommy "kamar yadda na fara fada miki Hajiya Sa'adatu, dan Allah ki kara hakuri, na san kinyi, na kuma fahimci concern dinki. Amma wanna hukuncin da kika yanke na kawo mana Safina yayi dai dai. Safina is now our responsibility. Ta zama yar mu insha Allah. Kamar yadda ba zamu so mijin Mufida ya wulakanta ta ba haka ba zamu bari Gidado ya wulakanta Safina ba. Duk abinda ya faru mu zakiyi holding accountable" ta sake juyawa kan Muhammad tace "kai kuma zamu gani in zakayi upholding mutuncin mu o zaka zubar da shi ka jashi a kasa". Muhammad yaji gabaki daya duniya tayi masa kunci, yaji kamar an zagaye shi da concrete an matse shi a guri daya. Numfashi ma da kyar yake barin kirjinsa. Yana ji Abba da Umma suka cigaba da bawa Mommy hakuri, suna ta lallashin Safina Mama har da jan ta jikin ta ta rungume ta tana ta kara bata tabbacin cewa ta zama yar ta daga ranar. Shi dai bai saka musu baki ba har suka gama, Sai da yaji an ambaci sunansa sannan ya dago kai, yaji Mama tana cewa ya tashi yaje yaci abinci "daga gain idonka tun breakfast din safe baka ci komai ba" ya tashi kamar robot ya je dinning table ya zuba abinci ya diba ya kai bakinsa, ji yayi abincin kamar ba'a saka gishiri a ciki ba. kamar ba'a saka gishiri a ciki ba. "I can cook. I can really cook" yaji muryar Safiyya a kunnen sa. Ya rufe idonsa a hankali yace "get out of my head" ya sake jin muryarta "zaka sha girki. Sai na koya maka cin abinci. Sai na mayar da kai kato". Ya cika katon cup da ruwa ya shanye sannan ya sake cika wani ya sake shanyewa. Ya sake jin shaidan ya kuma yi masa rada a kunne "in da zaka samu wani abu ka sha, zata fita daga cikin kan ka". Ya mike daga kujerar yayi hanyar waje sai yaji Abba ya kira sunan shi daga palo, ya juyo amma kafin ya karaso yaji ace "kaje waje ka jira ta ta fito ku tafi" "ya gyada kai yana kallon Safina sannan yace "to Abba" sai ya sake juyawa ya yi waje. Motarsa ya bude ya zauna ya kwantar da kansa tare da rufe idonsa. Trying so hard not to think of anything. Bai san minutes din da ya dauka a haka ba yaji an tayar da mota. Ya juya bayansa sai ya ga motar da yake tunanin a ciki Mommy tazo ce ta fita daga gidan. Ya mayar da kansa ya kwantar tare da sake rufe idonsa. 17 6 8:42 PM Ba'a jima sosai ba yaji an bude kofar motar da yake ciki an shigo, Ya kunna ignition din motar ya tayar da ita tare da saka reverse. Yaji tayi masa magana "salamu alaikum" va iuva va kalle ta, ta bude. tare da saka reverse. Yaji tayi masa magana "salamu alaikum" ya juya ya kalle ta, ta bude fuskar yanzu amma ba gabaki daya ba but still he saw murmushi akan lips dinta. Sai da ya fita daga gate din gidan sannan yace "Ameen wa alaikumus salam". Daga nan ya cigaba da tukin motarsa. Tunanin da ya fara zuwa masa kansa shine gidan su fa zasu tafi ko? Gidan auren su shi da ita. Unbelievable. Shi tunda aka gama hidimar siyan gidan bai kuma zuwa cikin sa ba. Ko kayan sawa ma bashi da su a gidan ballantana kayan amfani. Duk suna daya gidan nasa inda ya zauna lokacin bikin. Sai da yayi circyiling around layinsu twice kafin ya kama hanyar gidan. Zuciyar sa zafi take yi masa amma yayi kokarin kwantar da ita dan samun damar samun amsa daga bakin da yayi targetting samun amsar from. Suka cigaba da tafiya in silence sannan yaji tace "kayi hakuri anyi maka fada saboda ni" bai ko nuna yasan tana gurin ba. Tayi kokarin cigaba da magana "ni ban san..... "Please, ina kokarin driving ne zan kai mu gida, if you continue talking to me, zamu iya tafiya lahira instead of gida, and I do not want to have your blood on my hands". Daga nan bata sake magana ba har suka je gidan, Yayi horn mai gadi ya leko sannan ya koma ya bude musu gate, suna yin packing mai gadin ya taho da sauri yana gaishe da Gidado sai kuma ya lura da Safina ita ma ya gaishe ta. Daga ganin yadda yake kallon ta. gaishe ta. Daga gain yadda yake kallon ta kasan tunanin wacece wannan yake yi. Shi dai yasan gidan amarya ne nan har ma anyi jere amma ba'a kawo amaryar ba, he expects in za'a kawo amarya za'a zo da motoci da mutane da yawa ana guda but wannan amaryar ita daga ita sai angon suka 20 a mota kamar masu zuwa unguwa. Yayi sauri ya tafi yana kunna fitilun gidan, sai da ya dawo sannan Muhammad ya tambaye shi key din cikin gidan dan shi kansa ba shi da su. Yazo ya bude ya shiga ciki yana kukkunna fitilun ciki suma. Muhammad part dinsa direct ya wuce ya shiga toilet yayi alwala, sai a lokacin ya lura da irin haduwar da gurin nasa yayi da irin kudin da iyayensa suka kashe a part din nasa. Yaji muryar Safiyya "inye! Rich kid!" Yayi murmushi. Shi kansa ya san shi dan gata ne, Allah yayi wa iyayen sa arziki sannan kuma ya sanya musu kaunarsa mai yawa a zukatan su. Shima kuma Allah ya sanya masa kaunar su a tashi zuciyar. Wannan shine concrete din da yaji ya takure shi a guri daya. Duk wani hukunci yanzu da zai dauka akan aurensa da Safiya will either mend or destroy relationships dinsa da su. Ya fito yayi sallar isha din da bai yi ba sannan ya sake daukan key din motarsa ya fice daga gidan, daya gidan nasa ya koma ya debo kayan sa da already ya riga dama ya hada su a waje daya tun ranar dinner, kayan da ya san zai bukata da gaggawa, ya zuba. ya san zai bukata da gaggawa, ya zuba su a mota ya rurrufe gidan sannan ya sake komawa can gidan. Mai gadi ya dauki kayan ya shigar masa da su ciki, sai kuma ya dawo yace "ranka ya dade Madam ce tazo kenan" bai ce masa komai ba sai ya kara da "Allah ya sanya alkhairi" Muhammad yace Ameen sannan ya shige ciki. Wanka ya shiga, dama abinda ya dame shi kenan, he took a cold shower kamar kullum sannan ya shirya cikin kananan kaya ya fito ya doshi part din Safina. Yana kokarin shiga ita kuma ta a kokarin fitowa da tray a hannun ta, saura kadan abinda yake ciin tray din nata ya zube sai tayi sauri ta matsa sannan ta ajiye tray din tana kallon sa tace "abinci da ma zan kawo maka. Naji Mama tana cewa bak aci abinci ba" Ya zagaye ta ya wuce ya zauna akan kujera sannan ya nuna mata kujerar can nesa da shi yace "sit!" Ta cigaba da tsaiwa a gurin da take kamar bata ji abinda yace ba sai ya mike a zuciye yana jin duk zuciyar da yake danne wa tana dawowa wuyansa, tayi sauri ta ja baya tare da hadewa da jikin bango jikin ta yana karkarwa idonta yana kawo kwalla, ya dakata few inches to her ya sake cewa coldly "I said, sit down!" 10 6 3 8:42 PM Ta rakabe ta jikin bango ta wuce shi sannan ta zauna akan kujerar da ya nuna mata, zauna akan kujerar da ya nuna mata, hawaye yana bin idon ta, ya koma ya zauna ya dauki kafa daya ya dora akan daya yana kallon ta yace "ki mayar da wannan hawayen, ba zasu yi miki amfani ba. Yanxu ina so ki fara magana, tun dazu na fahimci dama maganar kike so kiyi. Now you can do it. Ina so ki fara tun daga farko zuwa karshe. I want to know everything. About you and about Safiyya". Ta juya hannun ta alamar confusion tace "wacce Safiyyan? Ban gane safiyyan da kake magana akan ta ba" ya mike zaune sosai yace "Safina, sauran hakurin da ya rage min bai fi cikin tsokali daya ba, please don't make me loose it, please kar ki saka daga ni har ke muyi nadamar sanin junan mu, na roke ki" ya koma zaman da yake da, kafa daya akan daya, ya sake tambaya "who is Safiyya? Tell me about her" Tace "wallahi Muhammad.... ..... Ban gane wacce kake magana akan ta ba. Ina da cousin Safiyya, ina kuma da friends....." Yace "and you have a step sister called Safiyya, wacce kuka tashi a gida daya a daki daya kuka je makaranta daya kuka ci abinci from plate daya, wacce babanta ya rike ki tamkar shi ya haife ki, let's start from her. Tell me about her", He saw how she was struggling with the words sannan finally tace "she is my step sister" sai kuma tayi shiru, yace "I know she. is your step sister, besides, ni na fara tuna miki cewa she is your step sister. So tell me something I don't know. Like how she always discuss her boyfriend Muhammad with you and how you get my picture from her phone and send it to bloggers". Ta bude ido alamar mamaki "your picture?" Sai kuma ta fara juya kanta "wai kana so kace min kai ne wanda kuke waya da Safiyya? Wai kana so ka gaya min Safiyya ce ex din ka da ka gaya min about?" Ta fara wani sabon kukan. Yace "cut out that crap please. Ke karyar ki ma ko sallah ba ta yi" ta juyo tana kallon sa, thinking that Safiyya used the same words to insult her three days ago. Ta sake gwadawa "wallahi ba karya nake yi ba" yace "kamar yadda ba karya kike yi ba sanda kika ce min baki san yayanki Mustapha ba? Ko kuma sanda kika nuna min cewa baki san wasu twins ba? Ko kuma sanda kika ce min ke ba yar Kano ba ce ba?" Tace "to ai gaskiya na gaya maka. Ni ba yar kano bace ba. Both iyaye na yan Katsina ne and .." "And you think it is not important to mention to the person that will marry you that you were raised in Kano a gidan step father dinki, Idan da kin fada min hakan tun lokacin da muka yi waya ta farko we wouldn't be here discussing this, Instead you chose to lie and throw me a crap about ba'a Katsina kika yi makaranta ba. And Mustapha? Wannan karyar kuma fa?" Mustapha? Wannan karyar kuma fa?" Ta yi saurin dauko wayarta, desperate to defend herself tace "wallahi wanda kake magana akan sa ba yayana bane ba, cousin dina ne, ina da yaya Mustapha amma ba shi ba ne ka gani ranar nan a airport ba. I can show you yaya Mustapha a hoto. Ko kuma kaje gida ka neme shi ku gaisa. Ba karya nayi maka ba". Ya mike tsaye yana jin ransa yana kara baci, in ya cigaba da zama zaiyi abinda baya fatan ya taba yi a rayuwarsa, dan gab yake daya wanke fuskarta da mari. "Magana da ke bata da muhimmanci Safina. You will keep lying and lying. Ko da bashi bane ba the fact that I mentioned yayanki Mustapha, ya kamata ace kin nuna kina da yaya Mustapha, and then ki nuna kina da kanne yan biyu, in dai har da ace ke mai gaskiya ce" yayi hanyar waje sai kuma ya juyo yace"| will get my answers. Tunda na fahimci ba zan same su daga gurin ki ta dadi ba then I will get them somewhere. And I think I know where" Har ya kai bakin kofa ta kira sunan sa da karyayyiyar zuciya "Muhammad" ya juyo yana kallon ta baice komai ba sai tace "she is married" yaji kamar ta saka kibiya ta soki zuciyar shi, dai dai gurin da hope din cewa Safiyya karya take bata da aure yake, Yaji hope din yana dagargajewa yana bin jinin jikinsa. Daga yadda tayi maganar ya san cewa yanzu ba karya take yi ba. cewa yanzu ba karya take yi ba. 07 4 1 2 8:42 PM Ta mike tsaye suna fuskantar juna, ta fahimci cewa maganar ta ta taba shi sosai, ta sake maimaitawa "she is married" ya hadiye yaw yana jika dried makogwaronsa yace "married to who" ta cigaba da takowa zuwa gabansa tace "who Mukhtar. Her cousin Mukhtar. Wanda yake tamkar yaya ne a guri na nima". Ya ji jiri yana neman dibansa. Sai ya jingina da jikin kofar, trying so hard to hide his weakness from her. She saw that she got his attention and she continued talking "ka yarda da ni, ka yarda da rantsuwar da nayi maka. Ban san kai saurayin Safiyya bane ba. Nasan tana tare da wani guy da take yaudara a school, but she never show me you. In dai har kasan Safiyya da gaske kamar yadda kake claiming a santa, then you should know how secretive she is. She never let people in" ya sake hadiye abinda yaki tafiya a makogwaronsa yace "she let me in" tace "really? In har da gaske she let you in then ya kamata kaima ace ka san ni. As her sister that she spent her entire life with, ya kamata ace ka san ni. In har kai baka sanni ba, me yasa zaka ki yarda cewa ni ban sanka ba?" Ya matsa daga jikin kofar sannan ya bude ta ya fita. "Mukhtar" ya fada a hankali. "Mukhtar" ya maimaita. Safiyya •• LTE owner Episode Twenty Five: The Interview 2 Paid Advert *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad.* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*, *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332*. Not Edited Dakin sa ya wuce direct yana zuwa ya kashe. Dakin sa ya wuce direct yana zuwa ya kashe fitila ya kwanta ya yi addu'a ya rufe idonsa. Baya son yayi tunani. Baya son ya saurari maganaganun da zuciyar sa take gaya masa. Ya kai wajen mintuna talatin a haka sai kuma ya mike ya zauna. Kwakwalwar taki hutawa, babu abinda take yi sai bitar maganganun da suka yi da Safina da zu a falon ta. A maganganun da suka yi dazun ya kara tabbatar da abinda ya riga ya fahimta tun kwanaki uku da suka wuce akan Safina, makaryaciya ce, yanzu kuma ya kara fahimtar wani abu daban, munafuka ce, sai dai kuma a cikin jerin karairayin da tayi masa yau tayi mentioning something da ya fahimci cewa gaskiya ne, that Safiyya is married. The fact that Safiyya is married shattered all the remnants of hope da tunanin cewa she is not ya fara saka masa a zuciyarsa. But saying that she is married to Mukhtar raised another question a zuciyarsa. Ya san Mukhtar, ya hadu da shi a lokuta da dama amma basu taba exchanging words ba ko da kuwa sallama ce. But Mukhtar cannot be married to Safiyya musamman a lokutan da suke haduwar, no real man will allow his wife to openly have a relationship with another man a gabansa ba tare da ya dauki wani mataki ba, and Safiyya couldn't be married to Mukhtar and be staying in hostel while yana zaune a garin, yana zaune a garin. But Safina seemed censire when she mentioned Mukhtar's name. Kamar ba karya take ba but it doesn't seemed right. It just cannot be. Sun sha yin maganar Mukhtar da Safiyya. Ya taba ma kokarin nuna mata cewa Mukhtar yana son ta but she denied it. Sai dai kuma ya fahimci ta san hakan ita ma da kanta. And she later told him that Mukhtar yana daya daga cikin dalilan da yasa ba zata kai su gurin Uncle Ahmad ba. Sai dai ta kaishe direct gurin Daddy. Ya lissafa options dinsa, abubuwan da yake da tabbas akan su kamar the fact that Safina and Safiyya are step sisters and that Safiyya is married, sai kuma wadanda bashi da tabbas a kansu, kamar cewa Mukhtar shine mijin Safiyya. And then abubuwan da yake so ya sani kamar what happened to cikin jikin Safiyya, shin na gaske ne ma ko akasin hakan. And then the most important question "what happened to Safiyya?" Ya koma ya kwanta still yana hango fuskar Safiyya a gurin dinner din su. She lost all her glow, her aura, and her radiant smile. He could tell from her eyes that she is deeply hurt, "Careful, ni matar aure ce" Ya tuna kalmominta da yadda suka soki zuciyar sa, zuciyar sa. Ya tuna ganin da ya sake yi mata yau a cikin motar Mukhtar, bai kalle ta sosai ba but she still looked deeply sad kamar wadda kowa na duniya ya juya mata baya. And sai yaji babu abinda yake so illa ya sake ganin ta, all he wanted a lokacin was to look deeply into her eyes and read the truth from there. Ko da basu yi magana ba, maybe in ya kalli idanunta, maybe, just maybe, zai iya dauke some of the burden from her heart ko da kuwa hakan zai yi crumbling tasa zuciyar. Ya tuna maganar da Safina ta gaya masa dazu "guy din da take yaudara" and he smiled. Yes, he had his moments of doubt akan soyayyar da Safiyya take yi masa especially ranar da ta yi replying all the messages da ya ringa tura mata yana rokonta ta bashi dama suyi magana, messages din da har yanzu ya san su suke haunting Mama, amma Safiyya tayi replying with "ni matar aure ce kuma ina matukar son mijina bana son abinda zai bata masa rai. Amma yanzu, after she appeared a gurin dinner dinsa looking like yar gudun hijira, ya san cewa ko ma me take ciki a rayuwar ta a yanzu tabbas tana son sa, 22 5 9:19 PM Kafin yayi bacci ya yanke shawarar next step dinsa, ya yanke shawarar gurin da zai samu next answer dinsa, He woke up exhausted, mentally exhausted, but also determined, mentally exhausted, but also determined. Bai fiti daga bedroom din sa ba sai da yayi wanka ya shirya tsaf yana tunawa kansa cewa rabon sa da abinci tun breakfast din jiya. Baya son ya kalli fuskar Safina da sanyin safiyar nan ballantana ta bata masa mood dinsa ta kuma yi tempering da tunanin sa, dan haka addu'ar sa sanda zai bude kofar bedroom din ita ce kar Allah ya hada fuskokin su har sai ya bar gidan. Sai dai kuma fuskar tata ita ce abinda ya fara gani yana bude kofar dakin. Tana tsaye a gaban dining table dinsa tana ta aikin arranging and rearranging dishes. Ta ci kwalliya cikin doguwar rigar da ta kama jikinta sosai ta bayyana shape da cikar cikakken kirjinta, ta kuma tsaya iyakacin gwiwarta, gashin kanta ya sha gyara daga gani yaci kudi. Ta dan tsorata da ganin sa, maybe bata yi tunanin fitowar sa a lokacin ba. Ya hade rai ya zuba mata ido da kallon tuhuma, Falon nasa sai kamshin turaren wuta, turaren jikinta da kuma abinci yake yi. Ta danyi murmushi tana jujjuya hannunta, yadda ya sha kunun ya hade rai ba karamin kyau yayi mata ba, His face looking as fresh and handsome as always, "Good morning Habibj" ta fada tana langwabe kai gefe. "Wa yace ki shigo min daki?" Ya fada da busashshiyar murya, "ta fara takowa zuwa inda yake da yanayin tafiyar da yake motsa duk wata halitta ta jikinta, "ba wanda yace in shigo, na ga dakin mijina ne shi yasa na shigo, bana bukatar iznin wani kafin in shiga. shigo, na ga dakin mijina ne shi yasa na shigo, bana bukatar iznin wani kafin in shiga dakin mijina" Wulakantaccen kallon da yake bin jikin nata da take nuna masa dashi, tun daga gashin kanta har zuwa kafafuwanta, irin kallon da yan gayu su kan yiwa abincin da suke ganin ko zasu mutu ba zasu iya ci ba, like "God forbid bad thing Ta dakata tare da sauke idonta kasa, feeling necked and degraded, ji take yi kamar ta rushe da kuka, kalma daya bai gaya mata ba amma kallon da yayi mata sai da taji dama duka ya saka ta a gaba yayi mata. Ya dauke idonsa daga kanta ya karasa inda ya ajiye key din motarsa ya dauka ya cigaba da tafiya zuwa hanyar waje, ta juyo tana kallon bayansa tace "Fita zaka yi? I thought an baka hutu a gurin aiki. You should be resting by now" bai ce mata komai ba ta cigaba "Abinci fa? You haven't eaten tun jiya. Please ka tsaya ka ci abinci kar ka fita da yunwa. Nayi maka abinci fa dan Allah ka tsaya ka ci abinci, tun kafin sallar asuba na tashi dan inyi maka shi, dan Allah ka tsaya", Sai da ya kai bakin kofa ya kama handle din sannan ta kira sunansa "Muhammad Gidado" ya dakata sannan ya juyo "don't! Please continue with your Habibi din da kika fara tunda bansan sunan waye ba but Muhammad Gidado is my name, and you are not worthy of pronouncing it", Daga gida wani eatery da ya gani a hanya ya shiga yaci abinci, sannan ya karasa sabon. shiga yaci abinci, sannan ya karasa sabon gurin akin sa, one of the branches of oil company of his father, in da a yanzu shine yake jan ragamar gurin while Abba yana cigaba da rikon head office din su, akwai kuma sauran branches da yake dasu in almost all the states of the country. Sai dai tun ranar da suka zo da Abba aka gama cike ciken takardu aka kuma gama introducing dinsa a gurin ma'aikatan gurin sai kuma aka bashi hutun aure, one month Abba ya rubuta masa da hannunsa, but a yanzu Gidado yayi deciding fasa yin hutun da kuma durfafar aikin da gaske. Wannan yana daga cikin matakan daya dauka na ganin ya rage wa kansa tunane tunane ya kuma kare kansa daga hudubar da shaidan yake yi masa. A office din ya wuni har 5pm sannan ya tashi, shima kuma dan dai shine lokacin tashi a office din amma ba dan haka ba zai iya cigaba da zama a can. A wuni dayan da yayi kadai a office din shi kansa ya san already da yawa daga cikin ma'aikatan gurin sun tsane shi saboda yadda ya azabtar da su, bai huta ba kuma bai bar kowa ya huta ba. 13 3 3 2 9:19 PM Da yamma yana fitowa gidan su Safiyya ya dosa, ya gama shirya abinda zai yi a can din. A bakin gate ya tsaya yayi horn sannan ya jira, mai gadi ya leko ta yar karamar tagar shi ya ganshi sai Gidado yayi masa alamar yazo, ya bude karamar kofa ya fito tare da gaishe da Gi [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Da yamma yana fitowa gidan su Safiyya ya dosa, ya gama shirya abinda zai yi a can din. A bakin gate ya tsaya yayi horn sannan ya jira, mai gadi ya leko ta yar karamar tagar shi ya ganshi sai Gidado yayi masa alamar yazo, ya bude karamar kofa ya fito tare da gaishe da Gidado "yallabai sannu da zuwa" Gidado. da Gidado "yallabai sannu da zuwa" Gidado yay masa murmushi, something that tun safe bai yi ba. "Ya aikin?" Ya tambaya "lafiya lau yallabai. Ka shigo da motar ciki mana, su Hajiyan duk suna nan aj" Gidado yace "no, ba shiga zanyi ba" mai gadi ya bude baki "yallabai Hajiya fa ranar nan tayi fada da ka tafi" Gidado yace "yau ai ba zata san nazo ba ko?" Maigadi ya gyada kai yana murmushi yace "ba zata sani ba yallabai, me ake bukata?" Gidado yace "dama twins nake nema, na bar daya waya ta a gida bani kuma da number din su a wannan wayar. Suna ciki?" Mai gadi ya girgiza kai "sun fita yallabai, tun safe basa nan. Kasan kananan samari, ballantana anyi sababbin mota, kullum suna yawo ba sa zama a gida" ya karasa maganar yana murmushi, Gidado yayi murmushin shima "na gane. Just in sun dawo ka gaya musu nazo ina neman su" mai gadi ya dauko wayarsa daga aljihunsa yace "to in baka number din daya daga cikin su mana, sai kawai ka kira su, watakila neman gaggawa kake musu" Gidado ya dauko wayarsa yace "Okay, hakan ma yay" maigadin ya nemo number din "bara in baka ta Hassan, anfi samun sa a waya, Hussein shi yanzu haka ma yabar tasa wayar a gida", Ya karanto masa numbers din Gidado ya rubuta sannan yayi masa godiya, ya saka hannu a aljihu ya dauko kudi ya mika masa hannu suka yi musabaha ya bar masa kudin a cikin hannun nasa, ya lura da yadda fuskar mai gadin ya yi haske da murmushi, shi ma ya mayar masa da murmushin sannan ya ja. ya mayar masa da murmushin sannan ya ja motarsa ya tafi. Gidan su ya zarce, babban damuwarsa a cikin duk wannan abin shine ya ga ya gyara tsakanin sa da iyayensa. Sai da ya jima a mota yana shakar numfashi da niyyar daidaita fuskarsa, baya son ya cigaba da bayyana damuwa ga iyayen sa, baya son ya cigaba da saka su damuwa. Ya shiga gidan da sallama, lokaci daya yaji yana missing Mufida da ya duba inda take yawan zama ya ga bata nan. Mama tana zaune da dan karamin Alqur'ani a hannun ta, suna haka ido yayi mata murmushi, sai da ta aki aya sannan yace "sannu da hutawa Mama" ta bishi da kallo kawai sai ya mike ya doshi hanyar dinning "akwai abinci? I am starving" tace "daga ina kake?" Ya na cigaba da tafiya yace "office, yau a can na wuni, I bet Abba will be impressed" tace "office kuma? Na dauka hutu kake yi, kuma ba gidan ka ya kamata ka tafi ya huta kaci abinci ba? Ni banyi girki da kai ba" ya juyo ya zagayo ta bayan kujerar ta ya sunkuyo yayi mata kiss a goshi, "I just miss you ne shi yasa na zarto nan. Kuma ina son inci abincin ki, at least dai once a day ai ba za'a hana ni ba" ya ga murmushi ya bayyana a fuskarta, shine dama abinda yake aiming for, ya sanya farin ciki a zuciyar mahaifiyar ta sa. Sai gata ta taso da kanta ta zo ta zuba mishi abincin "me yasa ka koma aiki?" Ta tambaya, "so nake Abba yaji dadi, ya jima yana son in karbi aikin nan, and naga babu. yana son in karbi akin nan, and naga babu wata gajiya a tare da ni tunda an kwana biyu da gama bikin". Ta zauna tana kallon sa yana cin abinci "ka ringa samu kana cin abinci sosai Muhammad, duk kayi baki ka rame" ya ajiye cokalin hannunsa yana kallon fatar hannun nasa kamar mai tabbatar da bakin da tace yayi, sai kuma ya jingina hannun a jikin fuskarta yace "still na fiki fari Mama" ta girgiza kai "ina! Ban yarda ba, ai fuska dama bata kai jiki fari ba" ta jingina hannun ta a jkin nasa "see? Na fika fari" yayi dariya. Su kan yi wanna musun lokaci zuwa lokaci shi da ita, ya fita fari amma bata yarda, in ya matsa sai ta ce shekaru ne suka saka tayi duhu. Sosai yaga ta sakar masa fuska tana yin murmushi, ya kuma ji dadin hakan. Suna nan tare Abba ya shigo tare da Haidar, ya taso yazo ya gaishe shi ya fara kokarin bashi labarin zuwan da yayi office yau amma sai yaji har labari ya iske Abban. Anan suka yi sallar magrib are sannan suka sake komawa cikin gida, ya fahimci suma iyayen nasa sunyi missing zama suyi hira da shi. 11 9:19 PM. sunyi hirar aiki sosai da Abba sannan sunyi hirar Mufida da Mama, Sai da akayi sallar isha Mama ta fara korar shi gida "ka bar yarinya ita kadai tun safe, Ka tashi ka tafi, Akwai abinda kuke bukata ne a gidan?" Ya girgiza kai, "no I don't think so, but zan tambaye ta inji" ya ga alamar Mama taj da din hakan, amma duk da haka sai ta kara. dadin hakan, amma duk da haka sai ta kara da "kar ka manta dai Muhammad, yarinyar nan amana ce a gurin ka, idan ka zalunceta sai Allah ya saka mata". Daya bar gidan ma ba gidan nasa ya tafi ba, gym din da yayi register da su jiya can ya tafi, baya son ya koma gida sai ya zama too exhausted to even think, baya son ya bawa kwakwalwar sa damar yin tunani, musamman tunanin Safiyya da Mukhtar a matsayin mata da miji. Bai koma gida ba sai da aka rufe gym din by 11. Yana zuwa gida ya wuce bedroom dinsa direct ya shiga wanka, a cold shower as always, ya fito da bathrobe a jikinsa da towel a kansa ya ganta. Tana zaune akan kujera a gaban mirror hannun ta rije da wayar ta tana jujjuya wa, idanuwan ta a kansa. Jikinta sanye da riga da wando silk na bacci, kana gani kasan babu komai a cikin kayan. Ya tsaya kawai yana kallon ta yana jin murnar all accomplishments din sa na yau tana tafiya tana barin zuciyarsa. Ta mike tsaye, "sannu da dawowa. Ina ta kiran wayarka tun safe ba ka dauka ba" yaji ransa ya kara baci ya zo da sauri ya wuce ta ya bude kofa "get out of my room! Wai ke wacce irin dakikiya ce? Wai in tambaye ki ma, anya sanda akayi rabon aji irin na mata kinje kin karba kuwa? Ko kuma dai masu rabon ba su baki bane ba saboda sun san you did not deserve it?" Ta juyo tana kallon sa, fuskarta kamar zata yi kuka tace "ka sa, tuskarta kamar zata yi kuka tace "Ka gaya min duk maganar da ka ga dama. Ko me kayi min nina jawo wa kaina. Amma aikin gama ya gama, ni da kai yanzu mata da miji ne until you say otherwise, and I bet ba zaka iya saying otherwise din ba because your parents will disown you...... ..." Yace "disown me? Akan ki? Me kike daukan kanki ne wai? Okay let me tell you something, you are here because I want you here, you are here as nothing but a ladder da zan taka in kai ga inda nake son kai wa. And don't think shamelessly exposing that thing you call a body to me will get to me. Now get out, and this will be the last time da zaki shigo min daki". Bata fita din ba still, ta cigaba da tsaiwa a inda take "you promised..... You promised me ba zaka wulakanta ni ba and you promised you will perform all your duties as husband, akan wannan promise din muka yi aure" yace "I made that promise to someone that I thought I can accept as a wife, someone that you pretend to be, kuma I intended to keep that promise, Amma daga ranar da na fahimci cewa ke ce, daga ranar kika yi loosing wannan alkawarin. Now please, don't open that mouth of yours again, out of my room I said" tana sake bude bakin nata kuwa ya koma da baya ya damko hannunta and dragged her zuwa bakin kofa sannan ya hankada ta waje yadda ya san ba zata ji ciwo ba ya mayar da kofar sa ya rufe. Ya jima a tsaye a tsakiyar dakin idanunsa a rufe, wannan yarinyar bata da class sam, shi bai taba gain tsiraici physically irin wannan ba. Na kammala shirin kwanciya baccin sa ya kashe fitila ya kwanta, sai a lokacin ya dauko wayarsa yay going through tarin missed calls da tarin messages din da akayi masa through out the day. Sai a lokacin yaga missed calls din Safina, sannan da message da ta tura masa da rana. "Ban san inda ka tafi ba, amma ina kewar ka. Allah ya kare min kai ya dawo min da kai gida lafiya. I love you". Yayi tsaki zai ajiye wayar kenan ya ga wani message din nata ya shigo, kamar a lokacin ta turo shi. "Wallahi Muhammad ni ba yar iska ba ce ba, kuma ni ba mace marar aji bace ba. Idan da ace ka san ni kafin wannan lokacin ba zaka taba tunanin wani namiji zai yi min irin wulakancin da kake yi min ba. Kaddara ce ta fada min, kaddarar son ka da Allah ya jarabce ni da shi, Da ace zan iya cire wa kaina da bamu zo wannan gurin ba, Amma na yafe maka, Saboda ina sonka kuma ina yi maka fatan rahamar Ubangiji", Ya kashe wayar ya ajiye sannan yayi addu'a ya rufe idonsa. Washegari just like jiya, sai da ya gama shiryawa tsaf sannan ya fito daga akin sa. Yana fitowa wanna karon ma ita ya fara gani a zaune a kan kujera a falon sa. Ya tsaya kawai yana kallon ta yana tunanin anya kuwa akwai zuciya a kirjin yarinyar nan? Already har ta gama shirya masa breakfast akan dinning ta kuma shirya jikinta cikin doguwar rigar atampar da aka yiwa dinki mai kyau kuma dai dai jikinta, ta yi dauri da dankwalin atampar, kijinta da abincin ta suna kamshi. "Ina kwana Habibi" ta fada, idanuwanta a kumbure, daga dukkan alama ta kwana tana kuka, bai amsa mata ba ya dauki key din motarsa yayi hanyar waje. Ta bishi a baya da sauri ta sha gabansa. "Whether kayi alkawari, ko ka fasa yin alkawari, ka riga ka karbi aurena. Kuma dukkan nauye nauye na yana kanka" ya zagaye ta ya wuce, har ya fita ya rufe kofa kuma sai ya dawo ya watsa mata kudi a jikinta yace "cook dinner, I am bringing guests". Da rana yana office ya kira number din Hassan da ya karba jiya. Hassan ya dauka sai Gidado yace "sunana Muhammad Gidado" Hassan yace "yaya good afternoon, ina yaya Safina?" Yace "tana lafiya lau, tana ta missing din ku, ina Hussein?" Yace "gashi nan. Yana lafiya lau. Ni ai bani da number din ka" Gidado yace "I know, shi yasa ni na nemi taka na kira ka, kuna kanne na amma ace bamu wani san juna sosai ba. I want to invite. bamu wani san juna sosai ba. I want to invite you two to dinner today, in babu abinda kuke y" Hassan da sauri yace "babu abinda muke yi. Zamu zo insha Allah" Gidado yace "good. Allah ya kaimu. Ina jiran ku", Ya ajiye wayar yana murmushi. He can't wait to see what information he can get out of these two guys. Ranar da wuri ya tashi ya je gida gurin mama yaci lunch, ranar ma sai da tayi masa gorin gidan sa ya kamata yaje ya ci amma sai ya gaya mata cewa zai ci dinner a can din ai, kawai baya son yayi missing girkin ta ne. Daga nan gym ya wuce and spent da rest of the day there. Sai da yayi sallar magrib sannan ya tafi gida, ya shiga yayi wanka ya chanja kaya ya fito a dai dai lokacin da motar Hassan take shigowa gidan. He watched them from his window a lokacin da suka jera suna tahowa cikin gidan suna hira, he remembered seeing them ranar daurin auren sa a Katsina, but they are not the boys he saw ranar da ya fara zuwa katsinan, but that doesn't change the fact that Safina lied. Gabansa ne ya fadi, kar dai yarinyar nan baya yi abincin nan ba? Cos he thought zata kawo part din sane, baya son shiga part dinta amma kuma baya so ya bata lokaci da su, zata iya shirya musu abinda zasu fada masa. Ya bude kofar part din nata ya shiga da sallama, suna zaune akan kujeru su biyun suka juyo a tare suna kallon sa, Hassan yace. suka juyo a tare suna kallon sa, Hassan yace "wow" Hussein ya dan dake shi yace '"masha Allah ake cewa" Gidado yayi murmushi yace "Amen wa alaikumus salam ake cewa" duk suka yi dariya a tare sannan suka amsa masa sallamar sa. Ya zauna a kusa da su yana kallon dining table dinta, babu alamar abinci a gurin, yace "ina take ne" suka daga kafada duk su biyun. "Muna ta sallama shiru" ya dauko wayarsa ya nemo number dinta and for the first time tunda aka daura musu aure ya kira ta, tana ta ringing bata dauka ba. Ya ajiye suka cigaba da hira da su Hussein, hirar mota da hirar school, nothing personal, yana son sai tana zaune zai musu personal questions dan ya ga response din ta. Ganin bata da niyyar fitowa kuma ya san shine ya kamata ya shiga ya kira ta ya saka dole ya mike, sai dai bai san ina ne dakin ta ba, and he really doesn't want to enter her room, Dakin farko ya fara zuwa yayi knocking sau biyu sannan ya tura kofar kadan yace "muna jiran ki fa. Ko wankan chanja fata kike yi ne?" Hussein yayi dariya. Gidado ya tura kofar sosai amma babu alamar mutum a cikin dakin. Ya rufe kofar ya koma daya dakin da yake can karshe, ya yi knocking shima sannan ya tura kofar da sallama, Tana tsaye a gaban mudubi da dan karamin towel a jikinta wanda bai wuce na goge fuska ba, Rabin kirjinta da rabin mazaunan ta duk a bayyane suke, da kwalbar turare a hannun ta tana fesawa, ta. kwalbar turare a hannun ta tana fesawa, ta juyo tayi masa wani kasalallen murmushi tace "minti biyu. Ina zuwa", 10 3 1 P 9:19 PM Yayi sauri ya ja da baya, sannan ya jawo kofar da sauri yana jin zuciyarsa tana bugawa da sauri. Wannan wacce irin masifa ce ya debo ya kawo gidan sa? Bai jima da zama ba ta fito, har da dogon hijab a jikin ta, sai kuma ta tsaya tana kallon twins da mamaki, suka hada baki "surprise!" Tayi dariya tana kallon Gidado "wai kune bakin dama? Kuma nufin ku nayi slaving kaina in the kitchen for?" Suka yi dariya suma, Hussein yace "Allah ne ya kamaki, dama ba kya yi mana girki, yau kuma zamu ci albarkacin yaya" Ta zauna suka gaisa sosai sannan ta tambayi inda zata kai musu abinci, Gidado ya daga kafada "ko ina ma" ta tashi tare da jan hannun twins "nayi muku girki ba zan kawo muku ba, ku zo muje kitchen ku dauko da kan ku" Gidado yayi sauri ya dawo dasu baya tare da girgiza kai "not gonna happen. They are my guest and will be treated as such" suka dawo suka zauna, Hassan har da daukan kafa daya ya dora akan daya yana mata dariyar mugunta, Amma ita ssi yanayin fuskarta duk ya chanja, zuwa lokacin ta tabbatar da cewa Gidado is up to something. Tana so ta kebe. Gidado is up to something. Tana so ta kebe da twins ta gaya musu suyi minding tongue din su amma babu dama. Haka ta debo warmers din abinci ta jera a kan dining sannan tayi musu magana suka taso, kuma tayi serving din su. Suka fara cin abincin in silence, Gidado yayi noticing how tasteless the food is, sai kamshi da ya cika gidan. Ya ajiye cokalin sa yana kallon Hassan, ya ga alamar yafi Hussein magana yace "to ya gida? Tell me about every one at home. Tunda ni ma na zama dan gida yanzu" Hassan ya gyara zama yace "a gidan mu dai the first rule is to never cross Mommy. In ta fara yi maka fada har sai kayi bacci ka tashi bata gama ba" Hussein yace "but she barks more than she bites. Fadan ne kawai da ita baya iya yi mana komai. Musamman ma mu yan autan ta" suka kalli juna suka yi dariya, Hassan yace "she is so loving, tana son mu sosai, she can put her life on the line for us" Hussein yace "amma Daddy! Kar ka sake ka bata wa Daddy rai, Zai babballaka ne kamar rake" Hassan yace "ka tuna wata damka da ya taba yi min? Sai da allon kafada ta ya goce" suka sake dariya, Muhammad kuma yayi murmushi. They are just like Safiyya have described to him. Muhammad ya rungume hannun sa a kirjinsa yace "and Safiyya? Should I cross her or not?" Safina ta ajiye spoon din hannunta ta zuba masa ido. Hassan yayi murmushi, from his smile ma zaka gane irin son da yake yiwa. his smile ma zaka gane irin son da yake yiwa Fiyya, yace "Fiyya is the nicest of us all. She is stubborn though" Muhammad yayi murmushi. Sai kuma yace "wow! You just said nicest. Meaning kunfi sonta akan Safina? Zaku fitar min daga gida na yanzu" Hussein yana kallon Safina yace "ita ma ai ta sani. Muna sonta ita ma amma munfi son Fiyya saboda ta fi son mu" Muhammad yace "koma dai menene, since they are both married now, mazajensu are now included in the competition, ni kuma zan kwato u daga hannun mijin Safiyya. Waye shi ne wai? I should know him also" Hassan ya dan bata rai "yaya Mukhtar ne. He is our cousin. I do not like him. So na baka winner a competition din tun kafin a fara" Hussein yace "wannan mutumin bana jin ma zai bar mu muje gidan su in akayi bikin. He doesn't like us. Da shi da babansa". Muhammad ya juya ya kalli Safina da itama shi take kallo, ya sake kallon yan samarin da suke gabansa yace "in akayi bikin? You mean ba'a yi bikin su ba?" Hassan yace "ba'a yi ba ai, ka dauka anyi? Kwana daya ne tsakanin daurin auren ku da nasu, any naku Friday akayi nasu Saturday, Bata da lafiya shi yasa ba'a yi bikin ba sai ta warke" Muhammad yaji gumi yana tsatstsafowa daga cikin gashin kansa, Ya sake maimaita wa "you mean, last weekend akayi daurin auren Safiyya?" "Yes" suka amsa a tare. Ya mike tsaye ya zagaye table din amma ya. Ya mike tsaye ya zagaye table din amma ya rasa abinda yake nema, sai kuma ya bude fridge ya tsara a gabansa yana jin sanyin fridge din yana dukan sa, he wants to hold it together, he doesn't want to loose it, he wants to know more .... 9 > 1 9:19 PM Ya dawo ya zauna ya zuba ruwa a cup ya shanye, sannan yace "lallai Safiyya is truly an amazing woman, aure biyu kenan tayi in her young age" suka kalle shi with confusion a fuskokin su, "aure biyu kuma? Wannan shine auren ta na farko, Bata taba yin aure ba, Wa yace maka tayi aure?" Yaji wani abu yana kokarin tokare numfashin sa, but he couldn't stop asking, Yace "ita ta gaya min, I met her ranar nan, About four months ago, She was pregnant, We talked, And she said she is married", Ya fada yana kallon fuskokin su and immediately he mentioned pregnant he saw yadda gabakidaya yanayin su ya chanja, Suka kalli juna sannan suka kalle shi, they looked terrified kamar wadanda suka aíkata babban zunubi, Sannan suka hada baki suka ce "ba ita bace" "maybe wata ka gani" ya girgiza kansa, trying to press them more "ita ce, I am very sure of that", Hassan ya kalli Safina kamar mai neman taimakon ta, jin bata ce komai ba saí ya xe cikin rawar murya da inda inda "maybe she…she…... was pretending" ya taba. she.... ...She..... was pretending" ya taba Hussein "kasan yaya tana pretending to be pregnant was lokuta". Hussein ya mike tsaye "ya kamata mu tafi kar Daddy yace muni dare. Yaya Muhammad thank you for the invite. Yaya Safina thank you for the food " Hassan ya mike shima "yes, we should go. Thank you. Sai da safen ku". Daga Gidado har Safina babu wanda yace musu komai har suka fita daga falon. Bayan sun fita din ma sun jima a haka a zaune sannan lokaci daya Gidado ya mike ya dauki jug din glass din da yake gabansa ya rotsa da kasa. Ya dauki plate din da aka zuba masa abinci a ciki shima ya buga shi da jikin bango ya tarwatse. Ya tsallake mess din da yayi creating yayi hanyar waje a kokarin sa na hana kansa tarwatsa Safina ita ma da take zaune a gurin. Sai da ya kai bakin kofa sannan ta kira sunansa, ya juyo yana kallon ta da idon da take ganin kamar ba nashi bane ba tace "that answer you are looking for, you will find it in dai zaka cigaba da nema. But sometimes ignorance is merciful". Bai amsa ta ba ya bude kofa ya fita. Yes he will keep looking for the answer even if it will kill him. And he knows exactly where to look for it next. It is time to meet Daddy. Yes, a matsayin sa na surikin Daddy, ya kamata ya je ya gaishe shi. find it in dai zaka cigaba da nema. But sometimes ignorance is merciful". Bai amsa ta ba ya bude kofa ya fita. Yes he will keep looking for the answer even if it will kill him. And he knows exactly where to look for it next. It is time to meet Daddy. Yes, a matsayin sa na surikin Daddy, ya kamata ya je ya gaishe shi. Nafisa Tafida Usman Safiyya owner Episode Twenty Six: Face to Face M Paid Advert Contact Lame(07036662633)for all your costumes both oriflameand other special products that will make ur skin glow and flawless Kayanmu lamba daya ne wajen kyau da farashi daidai da aljuhun kowa. Muna Kano, muna aikawa kowanne gari. Muna tayaku zaben mayukan da zasu dace da fatarku. Sensitive skin Oily skin Dry skin, Haka nan duk yadda spots da pimples suka bata muku skin da zarar kun yi amfani da kayanmu zaku hue wanna takaicin da ikon Allah, Kayanmu tested & trusted, Skin care for exclusive women, Contact Aysha lame on My heart and thoughts are with my fans from Maiduguri, Allah ya shiga lamarin ku ya fitar da ku daga halin da kuke ciki. Allah ya mayar muku da ninkin abinda kuka rasa. Allah ya saukaka muku wannan rayuwa tare da mu baki daya. You are in my prayers always A Not Edited Motar shi ya shiga ya tayar ya fita daga gidan ba tare da ya san inda za shi ba. Babban abinda ya fahimta a maganganun da suka yi da twins shine karyar da Safiyya tayi mishi. Ranar da taje office dinsa ranar da tayi breaking up with him she lied to him cewa tana da aure a lokacin. She said "I am married. I have been married all along". Idan da ace haka kawai tazo ta gaya masa wannan maganar da ba zai taba yarda ba, da direct zai ce mata karya take yi, amma cikin da ya gani a jikinta a lokacin and the fact that sun kasance tare tsahon shekaru biyu da watanni amma bata taba kai shi gidan su ba duk kuwa da nacin da yake yi mata shine abinda yay convincing dinsa to some extent cewa da gaske take yi ita matar auren ce, But now, out of nowhere, he learned that karya tayi masa, But why? Sannan cikin da ya gani a jikinta kuma fa? Ya tuna da yadda yanayin fuskokin twins ya Ya tuna da yadda yanayin fuskokin twins ya chania the moment da yayi mentioning ciki, and then they lied that ai pretending take yi. Karyar ta su ma ko ma'ana bata yi ba. Why will she pretend to be pregnant just to break up with him? Zuciyar sa ta gaya masa amsar amma sai yayi sauri ya girgiza kansa, he refused to believe cewa bata sonsa, he refused to believe cewa yaudarar sa tayi, he refused to believe that Mukhtar take so a duk wannan tsahon lokacin. And even if, in the slightest chance that bata son nasa, me yasa tazo gurin dina din su looking and sounding so hurt. Ya tuna kalaman da ta gaya masa cikin dacin rai "you married my sister" she wouldn't be that hurt idan da bata son sa. Ya kuma tuna da kalaman Safina na karshe kafin ya bar gidan "sometimes ignorance is merciful" ya sake girgiza kansa, he doesn't want that mercy, he want to know, not knowing why is what is hurting him the most a cikin duk wannan drama din. Sai da ya lura kusan shi kadai ya rage a titi sannan ya juya zuwa gida, ya san cewa ba lallai ya samu baccin da yake bukata ba dan haka yana zuwa alwala yay ya tayar da sallah, asking God to put an end to his suffering and grant his heart peace, And then he found himself praying for Safiyya, for God to be with her and guide her akan dukkan lamurran ta. dukkan lamurran ta. Washegari weekend, bai tashi da wuri ba sai around 12, da ya tashi kafin ya shirya ya fito ya gama dukkan plans dinsa for the day. Matsalar sa ta farko kafin komai ita ce abinci, baya son yake zuwa gida gurin Mama cin abinci always saboda baya son ko kadan ta fahimci bai ji maganar su ba akan Safina, sannan kuma baya son cin abincin siyarwa, shi kuma ba girki ya iya ba. And there is no way da zai ke cin abincin Safina. Shi bai taba jin ma ya tsani mutum kamar yadda ya tsani yarinyar nan ba. Fita yayi wani mall a kusa da su ya lodo kayan kusa da baka. Kayan tea, cereals iri iri da dai duk abinda ya san zai iya ci without having to enter the kitchen. Ya zo ya lode su a cabinet din dining set din sa. Sai a lokacin ya lura da abincin da yake jere akan table din. Ya bude yaga farfesun kifi da kuma masa, ya tsaya yana tunani, shi bai taba ganin inda aka hada masa da kifi ba. 11 10 7 5 9:16 PM Gaya tea flask ya bude ya ga tea ne a ciki mai kayan kamshi, sai yaji kamar ya zuba ya sha amma kuma sai ya rufe, a fili yace "wannan mayyar fa zata iya zuba min asiri a abinci, dan naga alamar babu abinda ba zata iya ba", Ya dauko kettle a cikin kayan da ya siyo ya dafa ruwan zafi ya hada abinci yaci, a ransa yana mamakin yau bai ga mayyar ta shigo. yana mamakin yau bai ga mayyar ta shigo ba duk kuwa da cewa bai fita da wuri ba. Sai da ya gama ya dauko wayarsa sannan ya ga missed call din Mama, ya kira ta suka gaisa tace "na kira ai ashe baka tashi ba, sai na kira Safina. Dama ce maka zanyi tunda yau weekend ka shirya ka dauki Safina ku je ku gaishe da iyayen ka kuyi musu bangajiyar biki, sun sha hidima" yayi shiru yana jin plans dinsa suna tarwatsewa a gaban idonsa, yace "shikenan Mama, ina ganin gobe sai muje, yau da akwai wani gurin da zanje kuma already na riga na gaya musu zanje, suna jira na" ta dan yi shiru sannan tace "shikenan, Allah ya kaimu, amma Safina bata san zaka fita ba ko? Dan yanzu muka yi waya da ita har ta gama shiryawa kai take jira, tana ta murna zata fita yau" ya ji haushin zakewar Safina a gurin iyayensa yace "eh ban gaya mata zan fita ba, tunda ban san da wannan plan din ba" Mama tace "shikenan, ka je can din, cika alkawari ai yana da muhimmanci ga cikar mutuntaka. Amma ko gidan Mommy ne kuje kafin ka tafi din, in yaso sai ka bar ta a can ka tafi uzurin ka. Kaga Mommy bata ganta ba har yau, kuma maman Khausar ma naji tace gobe zasu koma Ankara, Turkey", Baya son ya kara cewa Mama no, dan haka yace "okay shikenan, zamu je can din". Amma a ransa sam baya son zuwa, baya son abinda zai distracting dinsa daga babban abinda yake gabansa, sai dai kuma ya san babu abinda yake gaban nasa wanda yafi. babu abinda yake gaban nasa wanda yafi biyayya ga abinda iyayensa suka ce. Sai da ya zauna a mota sannan ya danne horn din motar ya cika gidan da kara. Ba zai sake yin kuskuren shiga part din ta ba ballantana har ya shiga dakin ta da sunan neman ta. Shi ya san abinda ya gani jiya. And baya fatan sake gani. Yasan kuma tana sane ta nuna masa. Ya sake danne horn din, ya san har makota in bacci ma suke yi sun farka. Ta leko ta window "gani nan fa" amma tana rufe window din ya sake danne horn din. Ta fito da sauri ta a gyara mayafin ta. Lace ne a jikin ta riga da skirt da suka sha stone work, ta yafa mayafin da ya shiga da lace din, haka ma jakar hannun ta da takalmin kafar ta. Ta bude gaban motar ta shiga tana haki, "you could have at least called me kace in fito" ya watsa mata wani mugun kallo ya tayar da motar. Ta fara magana "Mama tace... ..." Yace "Please just shut it. Idan har kinsan abinda zai fito daga wannan ramin na tsakiyar fuskar ki ba answer din da nake bukata bace ba, to ki rufe shi, Bana son jin komai daga gare k", Tayi shiru ta juya kanta tana kallon side din titi yayin da suka dauki hanya. Sai kuma ta juyo fuskarta tana nuna bacin ranta tace "you know abinda nake gaya wa kaina kullum in kana min wanna wulakancin?..... Ya daga hannu "Please spare me. I don't know, I don't want to know and I don't care" ta kara jin haushi "okay, Kana da options guda biyu, ko dai ka sauke ni anan in kira guda biyu, ko dai ka sauke ni anan in kira Mama in gaya mata ka ki kai ni ko kuma kaji abinda zan gaya maka" ya kunna kida a motar tare da kure volume ya cigaba da tukin sa. Ta saki baki tana kallon sa, she never thought him to be this petty. Gidadon da taso was so warm and nice. This one is a monster that has no empathy. But she still loves him kamar ta mutu. Bata sake magana ba har suka je gidan. Gidan kakannin Gidado na bangaren uba. Suna shiga ya fara bin motocin da suke gidan da kallo, yana tantance su waye da waye a gidan, ga mamakin Safina sai ta ga ya juyo ya kalle ta yana murmushi yace "I know what? I am glad we came. Yau zaki tantance banbancin aya da tsakuwa, ma"ana, banbancin kaya masu daraja da kuma kayan bola". Ya bude kofa ya fita ya barta tana lissafin menene kayan bolan? And tun kafin ta shiga din sai taji ina ma bata zo din ba. 13 9 A 9:16 PM Ita ma ta lura gidan a cike yake da motoci, shin mutum nawa ne a gidan suka san cewa ita tayi cigiyar sa a social media tace tana son sa? Mutum nawa ne a cikin su suka san cewa baya son ta ya aure ta ne dan ya farantawaiyayensa? Ta bude kofar motar ta fita tana karewa gidan kallo, ba ta san ma ta kofar da zata. shiga gidan ba, and every thing in the house is screaming money and class. Ta hango Gidado yayi wajen wani magidanci da yake tsaye yana magani da wani teenager. Tun kafin Gidado ya karasa gurin su yace "Abdallah! I missed you kamar zan mutu" yaron yayi murmushin sa mai kyau amma sai taga maimakon ya amsa wa Gidado da kalmomi sai taga yana yi masa signing da hannu, amma daga alama Gidado ya gane me yace dan dariya yayi sannan ya karasa ya rungume shi a jikinsa, ita dai bata taba gain Gidado cikin wannan farin cikin ba. Sai kuma taga ya gaishe da magidancin "'uncle Faruk zamuyi kewar ku in kuka tafi". Ta tsaya tana tunanin taje ne itama ta gaishe su ko kuma ta shiga cikin gidan? A karshe dai ta wuce bata gaishe su ba ta shiga kofar da take tunanin nan ce hanyar shiga. A ranta tana cewa maybe ma baki ne ba wadanda ya dace ta gaisar ba ne ba. Sai da Gidado ya gama hirar sa da uncle dinsa Faruq wanda yazo kasar ne dama dan attending bikin kuma yanzu zasu koma Ankara shi da matar sa Huda, amma yar su guda daya Khausar zata sake bin Aunty Hafsat ne zuwa UK inda take karatu yanzu a can tare da cousin dinta Bassam dan Mammy kanin Al'ameen da kuma sauran yayan Aunty Hafsat, amma su sai next week zasu tafi, sannan ya shiga cikin gida. Falon ya tarar a cike, mostly da yammata da. Falon ya tarar a cike, mostly da yammata da samari, har Haidar yana nan shima. Ya ji a ransa kamar ya fasa zuwa inda yayi niyya ya zauna cikin yan'uwansa amma kuma baya son samun any slack a cikin plan dinsa, ya zauna a cikin su suka gaisa sannan ya tambayi Khausar ina Mommy take ta gaya masa tana dakin ta "tare da amaryar ka"' ta karasa maganar tana dariya. Sauran suna suka yi dariya. Ya mike shima ya tafi dakin Mommy din, kakar sa ta wajen uba. Ya tura kofar da sallama ta amsa masa, ya shiga yana jin dadin kamshin dakin da sanyin acn da ta cika shi. Tana zaune akan gado ta dora kafafuwanta akan cushion din da aka ajiye mata a gaban gadon saboda haka. Idanunta sanye da eye glasses, completely immaculately dressed kamar wadda zata fita unguwa. Safina tana zaune a kasa daga gefenta kanta a kasa. Ya shiga yana karewa dakin kallo "wow. Wai ke kullum cikin gyaran dakin nan kike? Sai kace wata amarya?" Ta bishi da harara "ina ruwanka to? Ko ka kawo gudummawar ka a gyaran dakin na wa?" Yayi murmushi "ai ni akayi wa gyaran na sani. Kuma na gani na yaba, Baki da problem, gurinki special ne a zuciya ta" ta kalli Safina da take gefenta ta tabe baki tace "ni kuma na ga haka, Zaka yi min dadin baki, Dama neman ka nake yi zo ka zauna anan" ta fada tana nuna gabanta, Ya karaso ya zauna yana jan yatsun kafafuwan ta", "Good afternoon momma, ya tsufa?" Ta rankwashi kansa, ya dafa gurin yana dariya, sai kuma ya ga ta kara bata. yana dariya, sai kuma ya ga ta kara bata fuska tana kallon Safina tace "amarya bamu guri zamu yi magana. Ki je ga iyayen ki can a sama ki gaishe su" Safina ta kalle shi, and he can already see yadda fuskarta ta yi loosing all the excitement da ta shigo gidan da shi" Tana fita Mommy ta bi bayan ta da wani kallo da Gidado ya san ma'anar sa sannan ta tabe baki tace masa "kai kuma bawan Allah duk iyayin ka anan ka kare? Anya wannan sangamemiyar matar ta ka bata fi karfin ka ba? Ina zaka kaita? Nonon ta daya yayi nawa duk biyun sanda ina budurwa". Gidado ya mike da sauri yana jin kamar ya fita daga dakin a guje dan kunya, ta jawo hannun sa, "dawo ai ban gama ba" ya dawo ya zauna ta cigaba "gaya min, a ina ka samo ta? na tambayi babarka tace min sun ce ka zaba a yan'uwa kace ba ka son yar'uwa. Kace kai kafi son bare. Me yasa?" Ya gyara zama yace "bani na samo ta ba ai Mommy, su suka samo ta, sai dai suyi miki bayani" yayi murmushi yana son chanja maganar "kar ki damu, ina da ke ai, And you are the most beautiful woman ever" ta tabe baki "ba ka son ta, I can see it in your eyes baka son ta, Da sake gaskiya, 17 9 9:16 PM Ba zan bari ta tsotse ka ba. Wannan dirkekiyar yarinyar sai ta zuke katas" ya kalli agogon hannun sa "zan iya tafiya yanzu? I. agogon hannun sa "zan iya tafiya yanzu? I have an appointment" ta dan ima tana tunani sannan tace "ie ka, I will think about your situation". Yana dawowa falo yaji shiru kamar babu kowa, sai da ya karasa shiga sannan ya gansu gabaki daya sun zagaye Abdallah shi kuma sai labari yake basu da hannunsa, kowa ya saki baki yana bin bayanin nasa, Gidado ya jingina da bango yana kallon su, wato Abdallah da yana da baki da kunnuwan su sun shiga uku fan a haka ma bai barsu sun huta ba, a cikin labarin ya fahimci hirar new abubuwan da ya tarar sun faru a gida wannan hutun da yazo yake basu, a ciki har da labarin amaryar yaya Gidado da yadda ta wuce bata gaishe da uncle Faruk ba. Sai kuma zancen Humairan Al'ameen tana da ciki Basma ma tana da ciki. Gidado yayi gyaran murya yace "Abdallah da kai mace ne mun shiga uku da tsegumi" duk suka juyo suka kalle shi suka yi dariya, banda Abdallah da bai ji me yace ba tunda lokacin da yayi maganar baya kallon sa, sai ya fara tambayar sa "what did you say" Gidado ya wuce shi yana murmushi bai bashi amsa ba, ai kuwa ya mike ya biyo shi har mota wai lallai sal ya gaya masa abinda yace, sai da Gidado ya tayar da motar sannan yace "in ka matsu ka zo gida na kayi kwana biyu, sai in gaya maka". Gidansa ya sake komawa ya sake shiryawa a tsanake. Yay shiga mai kyau ta alfarma irin. tsanake. Yayi shiga mai kyau ta alfarma irin wadda kullum yake da burin yi idan zai je ya gaishe da Daddyn Safiyya. Ko ta na nan? Ko zai ganta? Sai dai shi kansa bai san me zai cewa Daddyn idan ya ganshi ba. But he will surely ask some questions wadanda ba za suyi raising suspicious ba, and he will surely get some answers. A bakin gate yau ma kamar kullum mai gadi ya bude masa, sai kuma ya tsaya ya tambaye shi idan shigowa zai yi ciki ko kuma a waje zai tsaya. Ya gaya masa ciki zai shiga, bayan ya shiga ne kuma ya tambayi mai gadin idan Daddy yana nan. Mai gadin yace "Alhaji yana nan. Kasan bashi da lafiya. Bai fiya fita ba in dai yana gari sai dai in dole" Gidado ya gyada kai, indai har ciwon da Safiyya ta gaya masa yana damun Daddyn ta shine da gaske, then he should be in a wheelchair by now. Sai yaji wani tausayin Safiyya ya kara kamashi, in Daddy ya tafi zata zamanto babu uwa babu uba, and he should be the one to replace them all for her. Ya gaya wa mai gadin cewa gurin Daddy yazo, yazo ne zai gaishe shi. Sai maigadin ya shiga yace bara yayi masa magana, Ya jima sannan ya dawo yace "yace ka dan jira kadan, yana ciki yanzu, in ya fito falo sai ka shiga" har yayi gaba kuma sai ya juyo yace da Gidado "kar ka sake guduwa amma" suka yi dariya tare, Sai maigadin ya koma cikin inuwa kan kujerar sa ya zauna. Gidado ya bishi yaje ya zauna a kusa dashi yace "no. cikin inuwa kan kujerar sa ya zauna. Gidado ya bishi yaje ya zauna a kusa dashi yace "no gidan nan kullum na shigo sai in ganshi kamar dry, kamar babu mutane a cikin sa" maigadi yace "eh ai ba zama suke ba masu gidan. Tunda Allah yayi wa Hajiyar mu ta farko rasuwa Alhaji baya son zaman gidan nan sam. Sanda ya auri wannan Hajiyar ta yanzu kuma sai suka koma Kano da zama gabaki daya. Dama shi dan can ne" Gidado ya gyada kai "kana nufin mahaifiyar Safiyya kenan ko?" Mai gadin yace "eh ita fa. Anan suka tare ai tun farkon auren su. Anan aka haifi Safiyya, anan kuma Allah yayi mata rasuwa. Daga baya ya auri mahaifiyar Safina, su ai zuwa tayi dasu ita da Mustapha, kamar yan'uwa suke ai da mahaifiyar Safiyya da ta Safina, ban san dai dangantakar tasu ba amma tun waccan Hajiyar tana da rai wannan tana zuwa sosaj" Gidado ya bude baki zai sake next question dinsa sai ya ga wani dogon saurayi ya fito daga cikin gidan ya doso inda suke da murmushi a fuskar sa, Tun kafin ya karaso Gidado ya gane waye shi, suna yanayi da Safina da kuma twins, sai dai kamar yadda Safina ta fada, ba shine wancan Mustaphan da ya gani a Katsina ba amma still hakan ba wai yana nufin tana da gaskiya ba, 13 9:16 PM Ya karaso ya mika wa Muhammad hannu "Muhammad Gidado, welcome, ya amaryar?" Gidado ya kirkiri murmushi "lafiya lau, tana gaishe ku. Tayi missing din ku". lau, tana gaishe ku. Tayi missing din ku" Mustapha ya girgiza kai "ahh! I doubt much, yarinyar can ba zata yi missing din mu yanzu ba. Lokaci daya ta birkice mana ita aure ta ke so ita kai take so" ya karasa yana dariya amma Muhammad bai yi ba. Sai kuma yayi gyaran murya yace "Daddy yace ka shigo" suka juya suka jera zuwa cikin gidan, a hanya Mustapha ace "sunana Mustapha, kuma ni yayan Safina ne uwa daya uba daya" Gidado yace "I know" daga nan bai sake cewa komai ba. A kofar falon Mustapha ya tsaya, Gidado ya shiga shi kuma ya koma da baya Yana shiga falon Daddy abinda Gidado ya fara gani shine hoton wata mata yana facing dinsa, kallo daya yayi mata ya gane wacece, ya gane cewa ta jikinta Safiyya ta zo duniya. Tana tsaye da dan katakon award a hannunta, da murmushi a fuskarta, a jikin katakon ya karanto sunan ta "Safiya Khalid" yaji gabansa ya fadi, ya tuno sunan da ya gani a cikin biography din Daddy, wannan Safiyan suke nufi ashe. Ya sauke idonsa kasa ya sauke su akan Daddy, yana zaune akan kujera yana kallon sa, he looked just like pictures dinsa da yake gani a gurin Safiyya, except that he looked smaller and older now, daga alama ciwon nashi ya kara tsanani, Yayi kokarin tattara nutsuwar sa sannan ya durkusa daga dan nesa kadan da Daddy ya gaishe shi "Daddy barka da yamma" ya fada yana jin zuciyarsa tana matsewa with emotions, this has. tana matsewa with emotions, this has always been his dream a cikin shekaru biyu da suka wuce, now gashi a gaban Daddy amma kuma a matsayin mijin Safina ba wai saurayin Safiyya ba. Daddy ya amsa masa yana studying dinsa da sharp eyes dinsa da suka yi making Gidado uncomfortable "ya mutan gidan?" Gidado yace "lafiya lau Daddy" Daddy yace "Sa'adatu ta ce min ai kai jikan marigayi Muhammad Dikko ne ko?" Muhammad yace '"eh. Kakana ne shi" "mutumin kirki ne" Daddy ya fada, Gidado yayi murmushi yana jin dadi a ransa. Sai kuma ya tambayi Daddy "'ya saukin jikin?" Daddy yace "alhamdulillah Allah shine abin godiya. Never thought zan kawo yanzu, gani nan kuma har yanzu, sannan ban san yawan kwanakin da Allah zai kara ara min nan gaba ba". Daga nan sai Daddy ya cigaba da yi masa tambayoyi kamar inda yayi karatu da inda yake aiki yanzu da muka sauran affairs na rayuwa. Gidado da yazo da niyyar yin tambayoyi sai aka koma shi ake yiwa tambayoyin kuma yana amsawa da dukkan gaskiyar sa, Sai da ya gama sannan Daddy yace "nayi mamaki, Sa'adatu was complaining about you, Maybe you started on a wrong foot with her. Daga abubuwan da ta gaya min sai nayi picturing dinka a matsayin arrogant, rude and spoiled dan masu kudi, But you look and sound different. Na gamsu da tarbiyyar ka gaskiya. lyayen ka sunyi kokari. Allah yayi maka. lyayen ka sunyi kokari. Allah yayi maka albarka" Gidado yaji kamar an bashi award, ya amsa da "Amen Daddy, Nagode. Allah ya ja kwana ya kara maka lafiya". Ya sake daga kai ya kalli hoton Safiya, sai Daddy yace "she was my first wife. Ta rasu. Safiya sunan ta" Gidado ya sunkuyar da kansa yace "Daddy na dauka kanwar Safina ce Safiva. Ashe suna ta ci" Daddy yayi murmushi, he looked proud and in love. Yace "suna ta ci. Sanda na aure ta mun jima muna neman haihuwa Allah bai bamu ba. Mun zaga duniya neman haihuwa Allah bai bamu ba. Har mun fitar da rai. Sai kuma lokaci daya Allah ya bamu Safiyya. Sanda ta haife ta na bata zabin cewa ta saka mata sunan da take so. She spent entire two days thinking, ko bacci bata iya yi, har cikin dare maganar sunan yake yi, she wanted to name her Hadiza sunan mahaifiyar ta but then she had a sister called Khadijah kuma in ta saka Hadiza wai waccan Khadijan ita ma zata ce an saka sunan ta, and then there is the other sister Sauda, wai Saudan zata ce ita ba'a saka sunan ta ba",. Daddy yayi dariya "she was so dramatic. Duk sun mutu fa. Wai a lahira ne za'a yi wannan rigimar idan sun hadu. So I saved her the stress na dauki yarinya nayi mata huduba da sunan ta, Safiyya, nace ta gaya musu cewa ni na fi sonta akan su baki daya", 13 5 9:16 PM Suka yi shiru baki daya. Sai Gidado ya samu kansa da cewa "Allah yayi mata rahama, yayi. Suka vi shiru baki daya. Sai Gidado ya samu kansa da cewa "Allah yayi mata rahama, yayi wa abinda ta bari albarka" Daddy ya gyada kai yace "albarka kam alhamdulillah. Dama ita mai albarka ce. Duk abinda ta taba albarka ce da shi. You know how some people are just blessed beyond measure, but then they get tested kuma up to their breaking point. In aun ci jarabawowin then they emerge stronger and wiser, in kuma sun fadi then they crumble and turned to dust". Gidado yayi shiru yana kallon Daddy cikin rashin fahimta, ya kasa gane yana magana ne akan waccan Safivan ko kuma abin da ta bari din "Safiyya". Muhammad yay kokarin throwing one of his questions "jiya ai muna tare da twins, su suka wayar min da kai akan Safiyya. I thought ta jima da yin aure a" Daddy ya jiyo yana kallon sa kamar mai studying dinsa, sai Muhammad yaji duk ya tsargu, har yayi tunanin Daddy ba zai amsa question din tasa ba sai kuma yaji ya yi magana "last weekend aka dauka mata aure. Yau sati guda chif kenan. Though ta jima ta na son yin auren. Ta jima tana yiwa Mommyn su magana, har daga baya ta ajiye kunya tayi min magana da kanta. But 1 had plans for her sai naki bata goyon baya" yayi ajjiyar zuciya "komai da da lokacin sa., Yanzu ne lokacin auren nata yay" Gidado yayi shiru yana digesting maganar, Sai kuma Daddy ya ajiye waccan maganar, daga alama ya tuna da wa yake magana, sai daga alama ya tuna da wa yake magana, sai ya dauko nasiha akan zaman aure da hakkokin mata da suke kan mijinta. Yace "ba ka da matsala da Safina, tana da hakuri sosai, bata da gardama musamman kuma tunda ita tace tana son ka tabbas zata yi maka biyayya iya kacin iyawarta. Da dai Safiyya ce.." Sai kuma yayi murmushi "ita wannan taurin kai ne da ita. She is always a handful" ya fada amma fuskarsa tana reflecting soyayyar da yake wa Safiyya. "'Amma Safina ban taba jin abokin fadan ta ba, ko da Safiyya ban taba jin suna fada ba. Bata ma da surutu sosai. Amma Safiyya in tana gida sai ta damu kowa a gidan. In kaji Sa'adatu tana fada to da Safiyya take y" ya sake yin murmushi sannan yay ajiyar zuciya "those are the good old days". Jin yayi shiru sai Gidado yace "ya jikin nata? Safina tace min bata da lafiya" Daddy ya juyo yana kallon sa "me tace maka yana damun ta?" Gidado ya danyi shiru yana tunani, Daddy sounds defensive, sai yace "she didn't say. Na dai ce bamu taba haduwa ba sai tace min bata da lafiya shi yasa" Daddy yace "eh, amma taji sauki sosai" and out of nowhere sai kuma ya dauki wayarsa yace "bara in kira maka ita sai ku gaisa, Tunda tafiya zamu yi*,. Gidado yay shiru yana saurarar Daddy yana magana, he was great full bai kira shi da matsayin mijin Safina ba yace dai kawai tazo za'a duba ta, Maybe da ba zata fito ba, But then kuma tunanin sa yana kan maganar. then kuma tunanin sa yana kan maganar tafiya da yaji Daddy yace zasu yi? Ina zasu je? Daga nan suka cigaba da magana, ya fahimci Daddy baya iya hada sentence biyu a tare ba tare da sunan Safiyya ya fito a ciki ba. Mostly labarin yarintar Safiyya da Safina ne. Suna cikin magana aka bude kofar da Gidado yake tunanin cikin gida ta shiga aka shigo. Sai kuma takun ya tsaya daga bakin kofar bai karaso cikin falon ba. Gidado ya daga kai, duk da wata zuciyar tana gaya masa not to look, matar aure ce, but he did looked and saw her. Tana tsaye a bakin kofa jikinta sanye da dogon hijab, kumburarrun idanuwan ta a kansa. She looked very thin and fragile, kamar in aka taba ta zata balle, and the eyes, the eyes are a clear testimony that she have been crying a lot. Yaji kamar ya mike ya je ya jawo ta jikinsa ya tambaye ta abinda yake damunta, he can do anything, anything, to take her pain away. Her A guje Mukhtar yake tafiya da mita yana ratsa traffic, gashi dama yanma ce gari ya cika da motoci, and in my heart hoping nake zai je ya buga motar a wani guri duk mu mutu, ko kuma ni in mutu, Amma bai buga mutu, ko kuma ni in mutu. Amma bai buga din ba. Ransa har lokacin a bace yake ina kallon yadda yake fitar da numfashi sama sama. 15 6 9:16 PM Ni ban san me yake yiwa gudu ba, tunda dai Gidado ba biyo mu yayi ba ballantana yace shi yake gujewa. Na goge hawayen fuska ta ina tuno da Gidado a gidan mu a tsaye a jikin motar sa. Ni na san ba guri na yazo ba, to menene ma hadi na dashi da zai zo gurina? Gurin matarsa yazo, zuwa yayi ya bawa Safina hakuri kamar yadda Mommy ta nema sannan ya dauke ta su tafi gidan su. Fully accepting the marriage. Naji duniya ta kara yi min zafi, I have went through the heartbreak of rabuwa da Gidado through I have always bottled up my feelings na kasa barin kaina inyi tunanin ciwon da zuciya ta take yi akan rabuwa da shi. But now I have to accept rabuwa da shi din and also accept him as mijin Safina. Mijin Safina for God's sake. Ta yaya zan jure ganin su tare a matsayin mata da mij? Ta yaya zan iya mantawa da shi bayan dole zan cigaba da ganin sa around? Na kara duba possibility din barin Nigeria, But can I? Dana barta ma da farko haka na hado kayana na dawo da kaina, Yanzu ma in na tafi dawowar zan sake yi, Besides, it is a fool's choice to run from the battle field, Na juya ina kallon Mukhtar, what is he running from? juya ina kallon Mukhtar, what is he running from? Na sake gofe wahaye na nace "he is not following us, gudun me kake yi?" Yace "bashi na ke gudarwa ba. I do not give a P**** about him, kai na nake gudarwa, dan in ya tsaya yana kallon ki zan iya karya shi wallahi'" nace "ba guri na yazo ba, kuma ka sani, gurin matarsa ya z0. And I doubt idan zaiyi min magana ma ko da mun hadu" ya girgiza kai "ko da bai yi miki magana ba I can't stand having the two of you together in the same place. Zuciya ta ba zata tsaya guri daya ba. And I may do something that all of us will regret". Nace "now, you are doing something that you will regret. Daddy yace ka kaini gida straight. And I am sure yanzu ya tabbatar ba gida muka tafi ba, or yaji labarin mun shigo mun fita. Or really don't want to cross Daddy" yayi slowing down yace "ba zai ce dai ya fasa aura min ke ba ko?" Nace "yes, zai iya cewa" ya danyi murmushin da ban gane ma'anar sa ba yace "I think you are forgetting cewa an daura, Ke a yanzu iko na ce ba tasa ba" naji raina ya fara baci nace "igiyar aure ba zata taba limiting Daddy from me ba, Now, ka mayar da ni gida in ba haka ba Daddy zai fahimtar da kai abinda nake nufi idan baka gane ba". Ya juya kan mota ya dauki wani titin yace "not now. Har sai na tabbatar wancan banzan ya bar gidan can" naji raina ya kai. "not now. Har sai na tabbatar wancan banzan ya bar gidan can" naji raina ya kai kololuwar baci nace "sauke ni a nan" yayi kamar bai ji ni ba na sake maimaita Wa "Mukhtar ka sauke ni anan nace. I don't want to be in your car one more second" yace "saboda nace masa banza? You think ba banzan bane ba? Shashasha irin sa" Na kama handle din kofar na bude shi sannan na tura kofar a lokacin da motar take cigaba da tsalala gudu. Cikin seconds abubuwa da yawa suka faru, iska ta fincike ni waje sai kafafuwana ne kadai a ciki yayin da motocin da suke kan titi suka cika titin da horn. Mukhtar ya saki stirring motar ya baro seat dinsa gabaki daya sannan ya damko rigata ya rike da karfi ya hana kaina reaching kan titin, tare da kokarin tsayar da motar ta hanyar dauke kafarsa daga kan accelerator, sakin stirring da yayi ya saka motar mu ta sauka daga kan lane din mu ta hau daya lane din sannan ta gangara gefen titi. Sai a lokacin ya samu nasarar tsayar da motar ta hanyar taka break a hankali, sannan ya jawo ni ya dawo dani sosai kan seat dina, Ya tsaya yana kallona yana mayar da numfashi da sauri, na koma na kwanta a jikin seat dina tare da rufe ido na. Cikin fada yace "what?! What just happened? You want to kill yourself saboda na zage ship" Ba tare da na bude ido na ba nace "now you know" ya daki motar cikin dacin zuciya "why? Just tell me why kika zabi aure na when you know you love him this much, Me yasa ba know you love him this much. Me yasa ba zaki gaya wa Daddy directly cewa shine uban dan ki ba and have Daddy get you two married. Me yasa kika zabi dragging me into this mess?" Na bude ido ina kallon sa dusu dusu saboda kaina da yake juyawa nace "saboda ba shi ba ne ba. 12 9:16 PM And I will never stain his white" ya bude baki cikin mamaki "to ni kuma fa? Nine uban dan kike nufi ko menene? Why choose me?" Nace "saboda nayi addu'a and kai na fahimta a matsayin mijin da Allah ya zaba min. Now you have to accept me as I am or reject me". Sai yayi shiru yana kallona kawai, fuskarsa tana nuna tsananin bacin ransa. Na kwantar da seat din sannan na kwanta na juya masa baya, at that point ban damu da yaushe zai mayar da ni gida ba. In yaga dama mu kwana a motar shine a ruwa ba ni ba. Naji ya zura hannunsa ta sama na ya jawo kofar ya rufe ta. Sannan ya tayar da motar muka cigaba da tafiya, ban bude ido a ba ballantana in san inda muke tafiya kuma ban damu ba, Abinda na sani kawai a lokacin shine dole in koma asibiti in cigaba da karbar anti depressants din da aka taba min prescribing watannin baya when I tried something like this, Sai da naji an bude gate sannan na bude idona, na fahimci gida muka dawo, na mayar idona, na fahimci gida muka dawo, na mayar da ido na na rufe har muka yi packing sannan naji yace "ki tashi ki shiga ciki". Na tashi na bude kofa na fita, na gane dabarar sa, so yake ya ajiye ni kawai ya tafiyar sa yadda Daddy ba zai ganshi ba ballantana yayi masa fadan dadewar da muka yi. Bance komai ba na juya nayi hanyar cikin gida shi kuma ya fara kokarin bude mota kenan naji muryar Mustapha yana yi masa magana "hey, Daddy yana kira" na wuce Mustapha na yi shigewata a raina ina tunanin su Muhammad da Safina sun tafi tunda banga motar sa ba. Sai dai ina shiga falo naga Safina a zaune, Mommy ma tana zaune ranta a bace, daga ganin ta kasan tayi fada har ta gaji. Ta juyo kaina "da aka ce kar kuje ko'ina ba ku ji ba kenan? Idan shi ba shi da hankali kema ba ki da shi?" Ban ce komai ba na samu guri na zauna, ina son in tafi daki in zauna ni kadai da tunani na ina kuma son inji yadda aka kare da Safina da Muhammad. Muna zaune Daddy ya shigo tare da Mustapha, shima nashi ran a bace, yana kallona yace "me na gaya muku kafin ku taho" bance komai ba Mommy tace "kai ma kasan laifin waye ai, kasan wa zaka yiwa fada ba ita ba" yace "ai nayi masa nasa, Ita ma da laifin ta. To ki shirya ki hada kayan ki, gida zamu koma, Kano zamu tafi dan ba zan yarda ya cigaba da zuwa yana batan rai na ba, Idan kin huta sosai kin warke sai a saka ranar biki" ni dai bance komai ba, sosai kin warke sai a saka ranar biki" ni dai bance komai ba. Mommy tace "ni ban ma fara tunanin nata bikin ba tukunna, wannan da akayi bikin ita ce nake so mu san matsayin ta first. Ni na kasa gane matar aure ce ita ko kuma budurwa?" Bai ce komai ba ya juya kujerar sa zai fita, Mommy tace "ba ka ce komai ba fa?" Ya juyo still da fada a muryarsa yace "cewa fa kika yi ba ya ta bace. Da bakin ki kika gaya min cewa bani na haife ta ba. Me kike so ince kuma? Kika dauki yarinyar kika kai ta inda basu san mutuncin ta ba suka vi mata auren da babu mutunci a ciki, sai yanzu kuma da abu ya kwabe zaki tambaye ni mai za'a vi? Ke zaki san abinda zaki yi a kai. Ko kuma ki mayar musu da ita katsinan su san me zasu yi. Ni ba zan saka baki a ciki ba" tace "'wato yanzu dan ni da kai mun yi hukunci ba dai dai ba cikin fushi shikenan sai yara su zama sune zasuyi paying price? Ni da ka nuna min bani na haifi Safiyya ba shikenan sai in ce na daina shiga lamarin ta kenan?" Yace "ke dai kika yi ba dai dai ba. No babu abinda nayi ba dai dai ba, saboda ban yarda cewa takurawa yarinya ta auri wanda ta fada ta sake fadar cewa bata son shi shine dai dai ba, Ko da ke kika haife ta ba zan bari ki takura mata ba" ya juya cigaba da tafiya, ni a lokacin damuwata ita ce lafiyar sa, maganganun da yake tayi sunyi draining dinsa, muryar shi tayi can kasa sosai. Sai da ya kai bakin kofar komawa part dinsa sannan ya juyo yace mata "ki dauke ta ki kaiwa iyayensa ita, ki danka musu ita ki kaiwa iyayensa ita, ki danka musu ita amana a hannun su, hukunci kuma ya rage nasu. Tunda an riga an daura ba zamu cigaba da rike ta a hannun mu ba. Ke kuma.." ya fada yana nuna Safina "duk abinda ya faru bayan nan sai ki kira mu ki gaya mana. Idan yafi karfin iyayensa sai mu sani, idan munga akwai cutarwa sai mu shigar da shari'a ciki" ya juya ya karasa fita 13 6 9:16 PM Anan dai Mommy ta zauna ta cigaba da fada zuwa lokacin na fahimci a gurin Mommy babu marar tarbiyya kamar Muhammad. Safina bata ce komai ba nima ban ce komai ba. Daga baya dai naga Mommy ta yanke shawarar yin abinda Daddy yace tace da Safina taje su shirya su tafi. Ina nan zaune har ta shirya ta fito cikin shiga irin ta amare, ina kuma zaune Mommy ta sa aka fitar da duk sauran kayan Safina da suka rage a gidan ta ce in ta kai Safina gidan iyayen Muhammad zata kai mata kayan nata gidanta, sannan suka yi min sallama suka fita, Na cigaba da zama anan kamar mutum mutumi har Mommy ta dawo, tana kallo na tace "na kai ta, Ai naga iyayen nasa sunyi masa fada sosai, Ya dauke ta ma sun tafi", Na mike na shiga daki na na rufe kofa, Daren was one of the longest dare in the history of my life, Kuka dai nayi shi har na gode Allah, Kwana biyun da suka biyo baya were one of the terrible days of my life. Nayi kuka Kwana biyun da suka biyo baya were one of the terrible days of my life. Nayi kuka iyakacin iyawa ta. A daren kwana na biyun ne ina shirin kwanciya bacci twins suka fado min daki hankalin su a tashe, na bisu da kallo sannan na kalli kofar da suka shigo "lafiya? Jikin Daddy ne?" Suka girgiza kai, Hassan yace "daga gidan yaya Safina muke" na zauna a gakin gado ina kallon su, trying to guess what happened. Hussein yace "dama kin san mijinta?" Na rufe ido na na bude nace "me ya faru? Me yace?" Hassan yace "tambayoyi ya ringa yi mana. I think mun saki baki da yawa. We told him an daura miki aure da Mukhtar last week" naji kaina ya sara jiri yana neman dibana, ban ce komai ba Hussein yace "He said wai auren ki biyu kenan, muka ce daya ne, and then he said. ." Sai yayi shiru, but na san karashen maganar, Hassan ya karasa "he said kin gaya masa kina da are three months ago, kuma ya ganki da ciki three months ago". Nayi shiru ina tauna maganar a raina sannan nace "and Safina? Me tace masa?" Hassan yace "bata ce komai ba, bata yi magana ba" na gyada kai na "alright, It is okay, Kar ku damu kanku, I will call her sai muyi maganar Na jima a zaune bayan sun fita ina going over maganar sannan a fili nace "what are you up to Muhammad? Me kake yi?" I was terrified cewa he is closer to the truth, but also relieved that yana yi min son da zai zauna yana magana ta a gaban matarsa. zauna yana magana ta a gaban matarsa. Duk da na san son ba zaiyi min amfanin komai ba, shima ba zaiyi masa amfanin komai ba. Tunda ni matar wani ce. Shi kuma mijin wata. But sai kuma anxiety ya fara kamani, Muhammad is digging, yana haka rami ban kuma san a wanne bangaren yake hakar ba. Ban san ta ina ramin nasa zai bullo ba. Ina tsoron kar ya haka ramin da zai rufta da shi. Washegari ina zaune da yamma akan sallaya ta bayan nayi kuka na na gama kamar kullum, sai Daddy ya kira ni yace inzo ga bako nan yazo zai duba ni. Na tashi na tafi da kumburarrun idanuwa na da dogon hijab din sallah ta. Ban san waye bakon Daddy din ba and I do not care what I looked like. Amma ga mamaki na ina tura kofa sai ganin Muhammad nayi a zaune a gaban Daddy, a picture that has always been my dream. Daddy and Muhammad together suna hira suna murmushi, But now he is here as min yar'uwata Safina, not as saurayina da zai aure ni, Maman Maama. Nafisa Tafida Usman Safiyya* owner Episode Twenty Seven: Safiya @ 43 Paid Advert Contact Lame(07036662633)for all your costumes both oriflameand other special products that will make ur skin glow and flawless Kayanmu lamba daya ne wajen kyau da farashi daidai da aljuhun kowa. Muna Kano, muna aikawa kowanne gari. Muna tayaku zaben mayukan da zasu dace da fatarku. Sensitive skin Oily skin Dry skin. Haka nan duk yadda spots da pimples suka bata muku skin da zarar kun yi amfani da kayanmu zaku huce wannan takaicin da ikon Allah. Kayanmu tested & trusted. Skin care for exclusive women, Contact, Aysha lame on. Safiya Wani bangaren na zuciya ta ya cigaba da gaya min in koma da baya, kar in karasa shiga, bangaren da ya kasance cike da tsoro da fargabar outcome din wanna haduwar, amma kuma dayan bangaren yana nuna min cewa zuwan nawa gurin zainiya dakatar da duk wata annoba da rashin zuwan zainiya haifarwa. Ban san ne suke magana a akai ba ban kuma san me zasu ce ba har sai an karasa gurin tukunna zan sani. Gabakidaya zuciyar tawa kuma yana yabawa boldness irin na Muhammad, ko kuma dan bai san cewa da ace Daddy ya san ko shi waye da tuni wata maganar ake yi daban. Ta ja kafarta a hankali ta karasa shiga ciki, still idonta akan Muhammad, so take ta tambaye shi me yake yi anan kuma me yake gayawa Daddy amma kuma babu dama. Sai dai ganin da tayi babu chanji a fuskar Daddy ya dan kwantar mata da hankali ta fahimci bai gaya masa wata magana da ta shafe su ba, Ta durkusa a kusa da kafafuwan Daddy tana fuskantar Muhammad amma kuma ta juya yadda Daddy ba zai kalli fuskarta ba tace cikin maganar motsa baki yadda Daddy ba zai jiyo ba "don't! Please", Bata sani ba ko Muhammad din ya fahimci abinda tace ko kuma bai fahimta ba, ta dai ga ya dauke idonsa daga kaina sannan ya mayar da su kasa yana kallon yatsun hannunsa, muryar Daddy ta ratsa falon "Safiyya, mijin Safina ne yazo duba mu, ba ki gaishe shi ba" na dan gyara muryata dan farki nayi tunanin ba zata fito ba nace "barka da zuwa. Ya iyalin?" Ya dago daga kallon hannun nasa ya kalle ni, yanayin fuskarsa gabakidaya ya chanja, ya danyi gyaran murya sannan yace "lafiya lau. Ya jikin?" Na sunkuyar da kaina kasa nima ina yin duk kan kokari na na daina kallon sa nace '"da saukj" sai kuma muka yi shiru gabakidayan mu. Sallamar Mommy ce ta ratsa shirun falon, ban dago na kalle ta ba shima kuma Muhammad haka. Ta ratsa ta tsakanin mu ta zauna a kan kujerar gefen Daddy sannan tace "da gaske ne kuwa ashe, Mustapha yace min kazo kana nan nace anya kuwa?" Ya gaishe ta ba tare da ya dago kai ba "Barka da yamma" tace "lafiya lau. Ka kyauta kuwa da kazo ka duba Daddy tun kafin mu tafi. Ina so dama in cewa Safina ta gaya maka hakan kuma ban fada ba ashe kana da niyya dama", Ya dago kai muka hada ido nayi sauri na dauke kaina gefe, bana son ganin emotions din fuskarsa, it breaks my heart, Ya fara kokarin mikewa "Daddy zan koma, Allah ya kara lafiya ya kaiku lafiya, Mommy Allah ya tsare hanya" Mommy tace "a'a, baka shiga ciki ba ai, ko ruwa ba ka sha ba". baka shiga ciki ba ai, ko ruwa ba ka sha ba" vace "babu komai Mommy, next time insha Allah" sai kuma ya tsaya yana kallona. "Safiyya ban sani ba ko zaki iya zuwa mota, akwai sakon ki da Safina ta bani in baki" na dago kai da sauri ina kallon sa cikin mamaki, his boldness is really on another level. Ya cigaba da tsaiwa yana kallona yana jiran amsa, Mommy tace "zata iya zuwa mana, ai dama ance ta ringa motsa jikinta. Safinan Safiyya kenan tsakanin su sai Allah". Naga bashi da niyyar tafiya sai na mike, sai da ya tabbatar na taho sannan yayi gaba na bishi a baya. Ina fita na ganshi a tsaye a bakin kofar, muka jera a muna tafiya a hankali amma babu wanda ya kalli wani ballantana yayi magana har muka je gaban motarsa muka tsaya. Wani tunani ne yazo min nayi ssuri na kalli hanyar gate. Na dawo da idona kansa naga ni yake kallo with his full attention, kamar mai kokarin karantar soul dina. 8 6 2 9:07 PM "What are you afraid of?" Ya tambaye ni murya can kasa, ban ce komai ba sai ya bawa kansa amsa "kina tsoron kar ya shigo ya ganmu ne? Mukhtar kike jin toro?" Na cire idona daga cikin nasa na sauke su kasa nace "he is my husband" yace "just as Safina is my wife" ya karashe maganar tare da huro numfashi daga bakin sa, a kokarin sana daidaita emotions dinsa. "I am so sorry Muhammad" na fada a hankali. "I have hurt you fiye da kowa a duniya, ban yi maka adalci ba" yace "yes, you have hurt me real bad Piya, but I am not here for the apologies, maybe zan iya accepting apologies din naki nan gaba, but now I am here for the truth. Did you or did you not lie to me about being married and being pregnant?" Na goge hawayen daya fara taruwa a gefen ido na nace "yes, I was lying. Karya nayi maka. Ni makaryaciya ce" ya girgiza kansa "you are not a liar......" Na katse shi "haka ne, bana yi maka karya. Amma a lokacin nayi maka. I lied to you. Bani da aure a lokacin nace maka ina da shi". Yayi shiru yana cigaba da nazari na. "A cikin wata hudu, you have moved from single to married and then back to single, then to married twice and then to married once. Wannan zan dauka Safiyya? Wanne zan yarda da shi? Okay assuming you were lying a lokacin, me yasa kika yi min karyar? And don't give me the crap about ba kya so na dan a lokacin ne zan kara tabbatar wa da cewa karya kike sake yi min". Na dago kai ina kallon shi, I saw bacin rai vividly written on his face, sannan nace "ina son ka Muhammad, more than you will ever know. But somethings are not just meant to be....." Ya katse ni "and who told you we are. know. But somethings are not just meant to be..." Ya katse ni "and who told you we are not meant to be? With whom are we supposed to be? Who am I supposed to be with? Safina?" Ya fadi Safinan da dacin rai, Na girgiza kaina "I don't know. Somethings are hard to explain. Dan Allah kayi hakuri", Ya girgiza kansa "I just can't believe this. You just told me you love me, and then you say we are not meant to be, in yi hakuri. Ni ban gane ba Piya. Ki gaya min what's going on. What happened to you? Please ki gaya min. Whatever it is we can get through it together. Let me share the burden with you please" na kasa cigaba da kallon sa na sauke ido na kasa, na bude baki da niyyar magana amma ita ma sai na kasa. A karshe sai na kare da cewa "I can't. I am sorry", Ya zagaya ya bude motar sa kamar zai shiga sai kuma ya buga murfin motar da karfi ya sake zagayowa inda nake, he looks very frustrated, daga dukkan alamu neman abinda zai daka yaji dadi yake yi. Na sake cewa "I am sorry" na nuna ni "if you say sorry one more time....." Sai kuma yayi shiru yana kallona na "just look at you. Duba ki 02 gani yadda kika zama. And you won't tell me me yake faruwa. You won't tell me me yasa kika yi breaking up with me. And you won't let me ask Daddy questions da zasu bayyana min gaskiya, You won't let me tell Daddy gaskiya, But then you said you love me., All I have to do now is guess, And you know what my guess is? My guess is that. know what my guess is? My guess is that guy Mukhtar ne ya shirya wani abu, shi ya saka akayi forcing dinki a gida akan lallai sai kin aure shi, shi yasa kika yi min karyar aure da ciki kika rabu dani because you are been threatened by him to do so. Ni kuma ba zan kyale shi ba. I will find out the truth whatever it is and I will. ...... ." Na mika hannu kamar zan rike shi sai kuma na mayar da hannun na rungume su a jiki na nace "'it is not Mukhtar. Shima auren nan ba plan din sa bane ba it just happened" ya dakata da maganar da yake yace "you are defending him? Idan ba shi bane ba to babansa ne, you once told me ba kya son inje gurin sa because he wants you to marry his son. Shi ya shirya wanna kenan? Ko kuma Safina? Safina can do something like this because she is a liar and a hypocrite" na girgiza kaina "'] don't know. I don't have answers a yanzu. Amma na yadda a hankali komai zai bayyana to me. Wannan ita ce kaddarar mu Muhammad, wannan ita ce jarabawar mu. I am ready to face mine. Kayi mana kokari dan Allah kayi facing ta ka. I believe ubangiji yana da dalilinsa na saka wa abubuwa su kasance haka". 8 15 9:07 PM Yace "are you telling me to accept Safina as my wife?" Nayi shiru ina jin ciwon ambaton sunan Safina da kuma wife da yayi a sentence daya, Sai kuma nace "I don't know, Kai kayi making decision na auren Safina, you deal with it", Safina, you deal with it" Muka yi shiru na dan lokaci sannan nace "you should go. We shouldn't be standing like this. Ni matar aure ce. It is islamically wrong",. Bai ce komai ba kuma ban kalle shi ba ballantana inga abinda zuciyar sa take ciki, na kara da cewa "I wish you best of luck. Good bye" still bai ce komai ba na juya ya koma cikin gida. Direct sama na wuce zuwa dakina, na daga labule kadan na ganshi still yana tsaye a inda na bar shi idonsa yana kan kofar da na bi. Sai kuma ya zagaya ya shiga motar sa ya ci taya ya bar gidan. Na saki labulen ina jin idanuna a bushe, a zuciya ta ina fatan kukan ya kare dan ni kaina na gaji da yinsa. Na zauna akan gado ina kallon carpet din dakin, my mind blind. Sai kuma na daga kai na kalli picture din da yake facing gadon nawa, picture din Ammi rike da ni a hannun ta akwance akan gadon asibiti, fuskar ta dauke da matsanancin farin ciki, Daddy ya taba gaya min cewa it was the happiest day of her life. Sai na samu kaina da mamakin yadda ta iya shiga cikin wannan farin cikin bayan duk abinda ya faru a rayuwarta? Bayan duk abinda ta rasa? Sai na tambayi kaina shin nima watarana zan iya kasancewa cikin irin wannan farin cikin nata? Ko shikenan na gama samun nawa share of farin cikin a rayuwa? Na sake daga kaina ina kallon ta nace a fili Na sake daga kaina ina kalion ta nace a fili "how do you do it? How do you looked beyond your sadness and find happiness?" Sai na lura da amsar tambaya ta a hannun ta, Ni, nice farin cikin ta a lokacin, she looked passed her past and into her future, sai na fahimci wani abu guda daya, idan har ina son samun farin ciki sai na daina hanging onto my past nayi planning future dina, and to plan my future sai na nutsu na daina kuka nayi making bold decisions. Just like she did. Sai na yi taking control of my life, just like she did. Na tuno da labarin da ta bawa Daddy, shi kuma ya bani, labarin decision din da ta yanke na barin garin su, na barin kowa nata, na barin komai nata, and starting a new life a inda babu wanda ta sani, babu wanda ya santa. But sometimes strangers are better than blood relatives. O Kafin Safiya ta bar gidan Hajiya Kyauta sai d [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Episode Twenty Eight: The Beginning of a New Life Paid Advert Contact Lame(07036662633)for all your costumes both oriflameand other special products that will make ur skin glow and flawless Kayanmu lamba daya ne wajen kyau. Sai washegari sannan ta samu damar assessing situation dinta da kuma mutanen da take tare da su. Yaran da suka taho dasu daga Gusau suma kananan yammata ne kamar ta. Biyu daga cikin su ma basu kai ta ba. Ta kuma fahimci cewa yanzu ta bar duk mutanen da ta sani, duk wasu wadanda suke da dangantaka da uta ta kusa ko ta nesa, yanxu ta shigo cikin mutanen da basu santa ba ita ma bata san su ba, babu kuma wanda ya san tana tare da su, hakan yana nufin zasu iya cutar da ita ta kowacce hanya in suka yi niyya. But she didn't care. It was a great risk, a bold step in her life, but she took it. Tasan cewa abubuwa biyu ne zasu iya faruwa a wannan gari na Abuja, ko dai rayuwar ta ta juya daga marar kyau zuwa mai kyau ko kuma ta chanja kalar rashin kyau din. Sai dai kuma Safiya bata ji toro a ranta ko kadan ba, wanne kalar shege ne rayuwa bata nuna mata ba? Bata jin akwai abinda zai far da ita wanda zai girgiza ta kuma. And she was ready to face whatever is coming her way, Ita dama ta saba making decisions a rayuwar ta, ta saba taking responsibilities, tun Baba Hadiza tana da rai sai da yawa Safiya ce take cewa ayi kaza ko kar ayi kaza and most of the times Baba Hadiza tana bin maganar ta ta ne dan ita din ta saba da bin umarnin wasu a tata rayuwar, dan haka yanzu Safiya bata da damuwar daukan responsibility and risks a rayuwar ta as she had nothing more to lose except her life, and to her, her life doesn't have much value. Sai da suka ci abinci a gidan suka yi wanka suka chanja kaya sannan Hajiya Kyauta ta zauna dasu ta fara yi musu bayanin aikin da za'a kai su suyi, wadansu daga cikin yaran already sun taba yin aikin a wani guri dan haka sun saba, Safiya kuma da bata taba aikatau na kudi ba itama ta saba da wahalar rayuwa dan haka bata jin cewa aikin zai gagare ta. "Babban abu mai muhimmanci da zaku rike a aikin nan shine tsafta, kunga mutanen nan yan gayun nan suna son tsafta ba sa son kazanta ko kadan, amma kuma basa son su wahala, dan haka babban aikin ku a gidan shine ku tabbatar da tsaftar gidan. Aikin da za'a baku ya danganta da gidan da suka dauke ku, wasu masu shara da wanke wanke kawai suke nema, wasu mai kula da yara, wasu mai wankin kayan yara da guga, wasu, wasu kuma mai girki. Ya danganta da hannun wadda kuka fada. In munje a gabanku za'a yi cinikin kudin da za'a ke baku, amma kuma ba ku za'a ke bawa ba, ni za'a ke bawa ina kaiwa iyayen ku. Duk Duk abinda ya faru a gida ni zan lira a sanar muku, kuma Icuma dulk abindia ya faru da lau ni za"a kira a gaya min. Duik wadida tayi sata ko munafunci ko zalunci za'a kore ta ta koa garin su babu ruwa na". Ita dai Safiya tana jinta amma a ranta tasan babu wani abu da zai mayar da ita garin su, ba zata koma ba ko da kuwa zata ke kwana ne akan titi Bayan sun shirya suka fita gabaki dayan su. Tun a gidan farko da suka je Safiya ta kara tabbatar wa da cewa ta shigo birnin tarayya, dan ita dai bata taba gain irin wannan gidan ko kuma makamancinsa a garin su ba. Suka shiga falon gidan suka zauna, sai da suka yi jira na gurin awa daya sannan matar gidan ta sauko daga sama, sai a lokacin ta tashi daga bacci. Ta zauna tana ta bata fuska da daga hanci sama kamar wadida aka ajiye mata kashi a gabanta. 10 9 115 AM "Hajiya Kyauta nace miki ki ringa saka yaran nan suna yin wanka sosai in zaki zo dasu gidan nan. Ni zuciya ta saurin tashi take yi wallahi". Hajiya Kyauta tace "ai kam sunyi wanka Hajiya, duk babu wadda bata yi wanka ba, sai dai kawai ace rashin turare kuma gashi mun shiga rana". Ta fara bin su da kallo daya bayan daya kamar mai zaben atampa a kasuwa sai ta nuna Safiya. "Waccan zaki bani. Tafi kvan gani'"., Hajiya Kyauta ta kalli Safiya tace "wannan banda ita, akwai yar'uwar ta a garin nan ita ta aika ni kauyen su takanas na dauko mata ita" Hajiyan ta bata rai "to ai kinji, ni duk sauran basu yi min ba gaskiya. Duk sunyi min kazanta da yawa" Hajiya Kyauta tace "to ai da sun kwana biyu anan zaki ga sun gyaru sun koma yadda kike so. Yanzun rashin kulawa ne ya saka suke haka" ta sake girgiza kai" gaskiya basu yi kin ba, in kin koma kya samo min wadansu wadanda suka fi wadannan kyan gani". A haka suka tashi suka fita, sai safiya ta samu kanta da tambayar kanta me vasa matar ta zabe ta bayan duk sauran yaran sun fita kyan gani? Suna fita Hajiya Kyauta ta kuma samar musu abin hawa tace "gidan Hajiya Maryama zamu fara zuwa gaskiya, in ba haka ba wahala zamuyi ta sha, in dai sun ganki cewa zasuyi ke suke son dauka" Safiya ta tambaye ta "me yasa?" Hajiya Kyauta tace "saboda kina da kyau. Shi ido yana son abu mai kyau, kuma shi abu mai kyau in yana guri yana disashe kyawun abubuwan da suke zagaye dashi", Sai Safiya ta samu kanta da mamakin haka, ita bata taba tunanin kanta a matsayin mai kyau ba, ita ba zata iya ma fasalta kan ta ba, ita ba ma zata iya tuna last time da ta kalli kanta a madubi ba. Ta san dai Baba Hadiza da Sauda da Khadijah suna da kyau. Sune mafiya kyawun halitta da ta sani a rayuwarta. Daga nan suka tafi gidan Hajiya Maryaman da aka jima ana gaya wa Safiya. Tun daga bakin gate din gidan Safiya ta fahimci gidan ya banbanta da daya gidan da suka baro. Shi wancan babu kowa sai mai gadi shi kadai, shi kuma wannan maza ne sun kai su hudu a bakin gate din suna hira. Daga can gefe ga wasu samari nan suna buga ball, a can karshen katanga kuma ta hango wata mata tana shanya kayan wanki. Wannan ya tabbatar mata da abinda Hajiya Kyauta ta fada cewa gidan mutane ne. Yanayin gidan katon gida ne a tsakiya, sai kanana a gefe da gefe, inda daga baya Safiya take fahimtar gurin yan aiki ne maza da mata. Suka gaisa da mutanen gurin sannan suka shige ciki. A cikin Safiya ta tsaya tana kallon haduwa da tsarin gurin, kujerun falon kadai abin kallo ne haka fentin, ga kuma sanyin ac da kamshin da ya ratsa su suna shiga, Yammata ta gani guda uku a falon a zaune suna kallo a tv, biyu akan kujera daya a zaune a gabansu, a shekaru ba zasu fi sa'annin ta ba amma a jiki sun kusa ninka ta saboda hutu da yanayin cimar su da ta banbanta. Yammatan suka tsaya suna kallon su kamar yadda suma suke kallon su, daya daga cikin su tace "lafiya? Daga ina? Kawai zaku shigo wa mutane gida ku tsaya musu aka kuna kallon su?" Hajiya Kyauta tayi murmushi tace "Hajiyan tana kusa? Munyi magana da ita tace min tana gida" dayar ta kan kujerar tace "tana nan, amma dan Allah kuje waje ku jira ta, in ta sauko sai ayi muku magana". Suka juya a jere suka fita kamar yadda suka shigo a jere. Suka je kuma suka jeru a baranda. Sun jima a haka sannan Hajiya Kyauta tace '"bara dai in kira ta a waya in gaya mata nazo, ba zamu yi ta zaman jiran tsammani ba" Jamila, daya daga cikin yaran da suke tare tace "to wai Hajiya su wadannan da suka koro mu waje yayan ta ne?" Hajiya Kyauta ta girgiza kai "sai dai yayan yan'uwa ko kanne, Allah bai taba bata haihuwa ba". Tayi ta kiran Hajiya bata same ta ba, har duk suka kosa, sai ga matar da suka gani tana shanya nan ta zagayo inda suke, suka gaisa da Hajiya Kyauta sai tayi mata bayanin cewa Hajiya suke son gani, matar ta shiga ciki sai gata sun fito tare da yarinyar da suka gani a zaune a kasa a ciki, matar ta fara yi mata fada "kina kallon mutane sunzo suna son ganin Hajiya sai ki bar su anan a zaune? Ba zaki shiga ciki ki duba musu ba? Kin fiso ki biyewa su Sa'adatu kuyi ta yiwa mutane rashin kunya ko? To wallahi kin san 15 5 1:15 AM halin Hajiya ko ki shiga hankalin ki ki kama kanki ko kuma ta sallame ki zuwa gidan iyayen ki". Yarinyar ta zumburi baki tana kunkuni ta koma ciki. Safiya ta fahimci yarinyar yar aiki ce. Bata jima ba ta sake dawowa tace "tace tana zuwa" matar ta ce "to ko ke fa? Yanzu ba ya fi ba? Amma wulakanta mutum ai babu dadi" sai kuma ta koma ta kawowa su Safiya ruwa, suka karba suka yi godiya, dama duk kishi suke ji. Matar ta cigaba da zama tare da su tana taya su hira, sai a lokacin Safiya ta san sunan sauran yammatan da suka taho tare dan babu wata maganar kirki da ta hada su a hanya. Suna nan zaune har Hajiyan ta sauko. Tun daga inda suke zaune a waje suka fahimci ta sauko saboda maganar ta da suka jiyo. "Waye ya bar remote akan kujera? Sai am zauna akan sa an balla shi" "Aka ce nayi baki, Ina bakin nawa suke?" "Aka ce nayi baki, Ina bakin nawa suke?" "Me suke yi a waje a cikin ranar nan?" Sai ga yarinyar dazu ta fito da sauri tace su shiga. Hajiya Kyauta ta dakatar da su Safiya tace su jira ta fara shiga suyi magana tukunna. Ta shiga suka gaisa sosai da Hajiya Maryama, "Hajiya ya kasuwa? Ya kuma fama da jama'a" Hajiya Maryama tace "lafiya lau. Ya taki kasuwar da naki jama'ar? Ina fatan dai kin kawo min yarinya mai hankali, kinga wannan Lawisan?" Ta fada tana nuna yarinyar da ta shigo da Hajiya Kyauta "rashin samun wata ne ya saka har yanzu nake zaune da ita, bata jin magana kuma bata girmama mutane, babu abinda ta sani sai kula maza, duk mazan can na waje samarin ta ne" yammatan da suke zaune akan kujera suka yi dariya, ta juya tana kallon su tace "ku tashi ku bani guri, ina magana kuna bin bakina da kallo kuna haddace abinda nake cewa" suka tashi sum sum suka shige ciki, ita ma yarinyar da aka kira da Lawisa ta tashi ta bisu. Bayan sun ta shiga ciki ne Hajiya Kyauta tace "na kawo miki yarinya Hajiya, musamman saboda ke na taho da ita Abuja" Hajiya Maryama ta gyara zama tace "alhamdulillah. Tana da hankali kenan sosa" Hajiya Kyauta tace "tana da hankali da nutsuwa, amma ba wannan ne dalilin da yasa na kawo miki ita ba, na kawo ta nan ne saboda ita marainiya ce ke kuma na san ke uwar marayu ce. Bata da uwa bata da uba, bata da danuwa shakiki ko daya, ba kuma ta da dangin uwa ko daya, sannan dangin ubanta basa kaunarta" sai ta bata labarin abinda ta sani a daga rayuwar Safiya. Hajiya Maryama tayi shiru tana tunani sai tace "kira ta in ganta inyi magana da ita tukunna" Hajiya Kyauta ta leka ta kira Safiya. Safiya ta shigo kanta a kasa tana kallon yadda kafafuwanta suke nutsewa a cikin carpet din falon da ta kasa tantance da me aka yi shi. Kamar da katifa kamar kuma da gashin rago. Ta durkusa daga nesa da su ta gaishe da Hajiya, Hajiya tace mata "ya sunan ki?" Tace "Safiya" Hajiya ta kalli ciwon da yake kafar Safiya tace "ya akayi kika ji ciwo haka Safiya?" Safiya ta dago kanta tana kallon ta tace "kusa na taka guda biyu, lokacin da nake kokarin tono yaruwata da katangar dakin mu ta fada mata". Duk hajiyoyin biyu suka bude baki, thinking about the trauma, dan itama Hajiya Kyauta bata san yadda mutuwar Sauda ta kasance ba, Hajiya Maryama tace "ina yar'uwar taki take to yanzu? An fito da ita?" Safiya tace "ta mutu. An fito da gawarta daga karkashin kasa, sal aka sake mayar da ita aka binne a kasan wata kasar a makabarta" suka sake yin shiru baki daya, sai kuma Hajiya ta sake tambaya "mamanki fa? Me ya faru da ita?" Safiya tace "Baba Hadiza, Mota ce ta kade ta, sanda take gudu zata cecemu ni da Sauda daga hannun Dauda" suka sake yin shiru, safiya ta kara cewa "Dauda din yayan mu ne" ba tare da sun tambaye ta ba, Sai Hajiya Maryama taji tana son jin cikakken labarin Safiya, ta tambaye ta, ita kuma ta bata labari tiryan tiryan a yadda rayuwar ta ta kasance tun daga kan abinda ta sani na labarin auren iyayen ta har zuwa rasuwar Alhaji Haladu da kuma tragedies din da suka biyo baya. 16 1:15 AM Bata san tana kuka a labarin nata ba sai da ta gama taga audience din nata suna share hawaye sannan ta share nata ita ma. Ta cigaba da magana "so nake in samu hanyar da san zamu jari in fara sana'"a, shine naje grin Hajiya Kyauta ita kuma tace min zata kawo ni nan in yi aikatau sai in tara kudin da zan yi jari dasu, Hajiya dan Allah ki dauke ni aiki, zanyi miki aiki sosai kuma zan ringa girmama mutane yadda ba zaki kore ni ba, in na tara kudi sai in gina wa Baba Hadiza masallaci in roki Allah ya gina mata gida a aljanna da ladan masallacin". Hajiya ta sauko daga kan kujerar da take ta durkusa a gaban Safiya tace "zan dauke ki aiki kinji? Kuma ba zan kore ki ba ko da kinyi laifi, in kinyi laifi zanyi miki fada in baki tarbiyya kamar yadda uwa ya kamata ta bawa yar ta tarbiyya. Kin zama yata daga yau kinji? Ina fatan nima Allah zai gina min katon gida a aljanna da ladan rikon da zanvi miki" Hajiya Kyauta ta share nata hawayen tace "Amen Hajiya. Dama nasan zaki karbe ta. Banyi tunanin kowa ba sai ke. Allah ya dubi niyyar ki ya baki ikon sauke wannan babban nauyin da kika dauka" Hajiya tace "Ameen. Ke ma Allah ya baki ladan taimakon da kika yi mata da zuciya daya. Da baki dauko ta ba da yadda zuciyar ta ta bushe din nan gudawar zata yi ko da kuwa an daura mata auren ne, kuma kinga da ba'a san hannun wanda zata fada ba". Ta juya gurin Safiya tace "zan dauke ki aiki, zan ke baki albashi kamar yadda bake bawa sauran yan aikin gidan nan, zanyi hakan ne saboda ki samu ki cika burin ki na gina wa mahaifiyarki masallaci da gumin ki, amma ba zan rike ki a matsayin yar aiki ba, zan rike ki a matsayin yata, Kuma ina so ki saki jikin ki, duk wata magana da kika san zaki iyayi da Baba Hadiza ki zo kivi da ni, in wata shawara kike nema ki zo gurina, duk wani abinda ya shige miki duhu ki tambaye ni, duk wani abu da kike bukata ki tambaye ni. Kinji?" Safiya ta gyada kai tana share hawayen ta, rabon da ayi mata magana with motherly concern irin haka tun Baba Hadiza tana da rai, hakan yasa ta tuna irin yadda take missing mahaifiyar tata. Daga nan sai Hajiya ta dauki wayarta ta yi kira, "Sa'adatu zo ina neman ki". Jimawa kadan sai ga daya daga cikin yaran da aka kora dazu ta fito daga ciki ta zauna a kusa da Hajiya tace "Hajiya ganj" Hajiya tace "ga yar'uwa kun samu ke da A'isha, ta zama kanwar u daga yau" Sa'adatu ta kalli Safiya ta a yatsina fuska tace "Hajiya yar'uwar mu kuma? Ji nake sabuwar yar aikin da aka kawo miki ce?" Hajiya tace "shi dan aiki ba mutum bane ba kenan? Ba zai zama dan uwa ba? So nake kuje ku samar mata kayan sawan da suka yi muku kadan a cikin kayan ku, da duk sauran kayan da kuka san zata bukata kafin in fita in siyo mata. A dakin ku zata zauna tare da ku saboda ina son ku kula min da ita, duk abinda tayi ba dai-dai ba ku gyara mata har ta gane ta saba da irin rayuwar nan. Kin gane?" Sa'adatu ta ce "eh" amma daga ganin fuskarta kasan bata ji dadin maganar ba, Hajiya ta kara sa da cewa "saura kuma kije kiyi tayi mata wannan fadan naki da baya karewa". Ta juya kan Safiya tace "wannan kanwata ce uban mu daya sunan ta Sa'adatu, daga yanzu ta zama yayarki. Zata ke kula dake kamar yadda yaya zata kula da kanwarta. Sai dai tana da fada" ta karashe maganar cikin tsokanar Sa'adatu da har lokacin take zaune fuskar ta a bace. Hajiya tace "ku je ki nuna mata dakin ku. Ta juya gurin Hajiya Kyauta tace "to sai kuma a bani yar aikin" Sa'adatu ta mike Safiya ta bi bayanta hannunta rike da ledar da hotan su yake ciki, wannan ledar ita kadai ce abinda Safiya ta shiga da shi gidan Hajiya. Wani dan corridor suka bi sannan suka yi kwana, sai suka tarar da kofofin dakuna guda biyu da kuma toilet a tsakiya. Sa'adatu ta bude kofa daya ta shiga sai Safiya ta bita amma sai ta tsaya a bakin kofa kanta a kasa. Babu abinda bata so a rayuwar ta irin a wulakanta ta, ta kuma lura kamar yammatan suna da wulakanci. Kallon dai suke cigaba da yi a dakin a tvn dakin. Daya yarinyar tana zaune a kan gado, Lawisa tana zaune a kasa, 6 3 1:15 AM Sa'adatu ta zauna akan kujerar dakin tace "Fati ga bakuwa nan inji Hajiya, tace zata zauna anan a wajen mu. Kuma zata zama kanwar mu" wadda aka kira da Fati ta kalli Safiya sannan tace "yar'uwar ku ce?" Sa'adatu tace "ni dai ban san ta ba, ban san a ina ta samo ta ba, tace kuma mu bata kayan sawa da abubuwan bukata" Lawisa da take zaune a kasa tace "yar aiki ce fa, na ganta tare da wannan matar da tazo" Sa'adatu tace "ina ruwan ki? Bana hanaki muna magana kina saka mana baki ba? Tashi ki fita?" Lawisa ta taso saura kadan ta bangaje Safiya sai ta bata guri ta wuce. Tana nan dai a tsaye Sa'adatu ta bude wardrobe din dakin ta fara debo kaya tana ajiyewa akan dago, sai data bata kaya sunfi set goma, har da mayafai da hijabs, sannan ta bude drawer ta bata sabulun wanka, tooth brush da paste, da kuma man shafawa da roll on da turare. Ta tsaya tana kallon ta sai ta kalli Fati tace "kuma fa kyakkyawa ce. Gyara kawai take bukata" Fati ta kalle ta ta tabe baki tace "fatan dai ba nan dakin zaki ajiye ta ba. Sai dai ki kata can dayan dakin" Sa'adatu bata ce komai ba ta saka hannu ta kwashi kayan tace "debo sauran mu tafi" Safiya ta debi sauran kayan suka fita suka shiga dayan dakin. Ta lura kamar dakin ba'a amfani da shi kamar wancan, amma kuma shima exactly kamar wancan din yake, Sa'adatu ta ajiye kayan akan dago tace "ga kaya nan na baki, ki zuba a cikin wardrobe din nan ki ki zuba a cikin wardrobe din nan ki ringa sakawa, ga kuma kayan gyaran jiki suma na baki, kin iya amfani da su?" Safiya bata ce komai ba sai Sa'adatu ta nuna mata yadda zata yi amfani da komai, sannan ta nuna mata yadda zata kunna kayan electronics din dakin, sai kuma suka fita ta nuna mata yadda zata yi amfani da toilet, daga nan ta mayar da ita falo. Sanda ta koma falo already Hajiya sun gama maganganun du da Hajiya Kyauta, Safiya ta fahimci Hajiya ta dauki Jamila aiki itama a gidan, amma instead of cikin gida da aka shiga da ita sai aka hada Jamila da Dije, matar da suka gani a waje, ta tafi da ita bangaren yan aiki mata. Hajjya ta tambayi Safiya in ta samu duk abinda take bukata, Safiya tace "ta bani kaya masu yawa, Nagode sosai Allah ya kara arziki" Hajiya tace "Ameen. Tana da kirki ai da kyauta, sai fada fal cikinta" Sa'adatu ta tura baki tana kunkuni. Daga nan suka yi sallama da Kyauta da sauran yaran, Kyauta tayi mata alkawarin duk sanda ta shigo Abuja zata je zuwa tana ganin ta, Ta tsaya tana kallon su har suka fita daga gate sannan ta juya ta koma ciki, A lokacin Safiya tana da shekaru goma sha hudu a duniya, dai dai da shekarun Baba Hadiza sanda aka aura mata Alhaji Haladu. A hankali Safiya ta fara adjusting to rayuwar gidan duk da dai ba xata ce babu challenges ba amma tana jin dadin changes din sosai. Ita kadai take kwana a dakin da Sa'adatu ta kai ta, and all the nights she misses her mother and siblings, wishing suma rayuwa ta basu irin wanna damar ta kwanciya a irin wannan gadon da kwana cikin ac a lafiyayyen dakin da baya zuba ballantana ya fada a kansu. Kullum ita take fara tashi a gidan, kafin kuma mutan gidan su tashi ta gyara duk inda take da access to, tun daga dakin da take kwana har falo har kitchen da duk wani daki da ya ke bude ko da kuwa babu kowa a ciki. So take ta nuna wa Hajiya irin gwanintar ta dan Hajiyar ta san bata yi kuskuren daukan ta aiki ba. Satin ta daya a gidan Hajiya ta dinka musu sababbin kaya ita da Jamila, sai dai na Safiya yafi na Jamila yawa. Ta lura su Sa'adatu suna zuwa makaranta, kullum da safe zasu tashi su shirya, Dije zata hada musu breakfast su ci tare da wasu samari biyu suma data fahimci rikon su ake yi a gidan, in sun gama driver zai kai su school, ita kuma zata je ta gyara musu dakin da suka kwana a ciki sannan ta wanke toilet din da suka yi amfani da shi, Farko ta samu challenges kafin ta iya aikin gidan, sai da Dije ta zauna tayi mata bayanin yadda ake yin amfani da komai sannan ta iya, a hankali kuma har ta kware. Ta fahimci cewa Fati yar kanwar mai gidan ce, ita kuma Sa'adatu kanwar matar gidan. 9 4 1:15 AM Ta kuma fahimci cewa daga mai gidan har matar gidan yan kasuwa ne kwararru dan har sunayin muamala sosai da kamfanonin kasashen waje. And she wished that one day she will be like them.... Jinin su yafi haduwa da Sa'adatu akan Fati, saboda Sa'adatu tafi fada amma tafi son mutane, Fati tana da rainuwa musamman da ta kara fahimtar cewa da gaske Safiya ba yar uwar Hajiya bace ba. A gurin Hajiya ma kuma tana samun kulawa ta musamman dan ko da yaushe in dai suka hadu sai ta tambaye ta "kin ci abinci? Akwai abinda kike so? Ki ringa yin bacci sosai kina hutawa ko kya samu ki dan yi kiba, ga Sa'adatu nan sai hawa take kamar fulawar da aka saka wa yeast". In Sa'adatu taji haka sai ta kara kumbura, Ranar nan tana dakin da su Sa'adatu suke tana yi mata tsifa, sun kulla kallo a tv suna yi ga wayoyi ana ta chatting da kawaye ana ga wayoyi ana ta chatting da kawaye ana shirya irin hidimar da za'a yi a birthday din wata kawar su da yake zuwa soon. Hajiya ta shigo ta tsaya a bakin kofa tana kallon su tana kuma jin irin hirar da suke yi ba tare da sun ga shigowar ta ba. Sai da suka gama sann6ta karasa shigowa ta kuma kama fada. "Kun ganku yaran nan sai kunyi wa kanku fada fa. Rayuwa ba zata tafi muku yadda kuke so a haka ba. Ku baku da tunanin komai sai na jin dadin duniya? Ya kamata ace zuwa yanzu kun fara tunanin yadda zaku ke juya biyar tana komawa goma. Rayuwa bata da tabbas. Kamata yayi ace kun fara tunanin wata sana'ar hannu ko wani kasuwanci da zaku iya fara wa tun kafin ku gama secondary school. Hausawa sunce da zafi zafi ake dukan karfe" Sai duk su biyun suka kwashe da dariya "haba Hajiya, wacce sana'a ce zamuyi ne wai? Sai kace wasu maza" "mu kam ai sai dai a nemo a kawo mana. Soft life kawai" Hajiya ta bude baki "soft life? Kawai dai kuce min cima zaune na tara a gida na. To Allah ya sawake muku. Amma dai sai kun sake tunani tun kafin lokaci ya kure muku, Ko irin dan cin cin din nan ne da zobo ku ringa yi mana kuna tafiya da shi makaranta kuna siyarwa" Sa'adatu tace "cin cin fa kika ce Hajiya? Haba dai! Wuce nan mana""Safiya dai bata ce komai ba har Hajiya ta fita, sai data gama tsefewa Sa'adatu kitson ta sannan ta fita tana neman inda Hajiya tayi, a falon ta na sama ta same ta waya da dealer din da zai kawo mata abayas. "A sabon shagona zan saka su, kaga kuma zuwa nan da two weeks nake son bude shi. Dan Allah kar saba min alkawari". Safiya ta zauna a kasa sai da ta gama wayar sannan ta kalle ta cikin kulawa tace "Safiya? Kina bukatar wan abu ne" Safiya ta gyara zama tace "maganar sana'a da naji kina yiwa su Sa'adatu. Kina gain nima zan iya yi?" Hajiya ta gyara zamanta tace "ba su Sa'adatu nake yiwa maganar sana'a ba, har da ke kema, gabaki dayan ku nake yiwa. Da akwai sana'ar da kike gain zaki iya farawa yanzu?" Safiya tayi shiru tana tunani sannan tace "a garin mu dai tun bayan rasuwar Baba ni da Baba Hadiza muna yin awara da kuma wake da shinkafa muna siyarwa, ban sani ba ko anan zasu siya?" Hajiya ta dan yi shiru tana tunani sai tace "gaskiya bani da tabbas din zaki yi cinikin wake da shinkafa anan, Amma ina saka ran zaki vi na awara tunda abin sha'awa ce." Ta sake yin shiru sai kuma tayi murmushi tace "kin san wani abu. I have a plan for you. Ki rubuta min duk abinda kike bukata na yin sana'ar awara ni kuma zan siyo miki. Zaki iya yin aikin dahuwar awarar a can filin baya, sai mu aika duk makota zan kuma yi miki talla a gun customers dina, sai a ringa sakawa a robobi ana aikawa ko'ina" Safiya tayi murmushi tana jin dadi "Nagode Hajiya, Nagode sosai " hajiya tace "and that is not all, zan bude sabon shagon da zan ringa siyar da fabrics na mata, da sauran ado na mata, zan dauke ki aiki a matsayin sales girl din shagon, zan hada ki da yarinyar da already na riga na dauka sai kuyi akin tare ki koyi harkar yadda ake gudanar da business" Safiya tayi shiru tana kallon ta tace "amma Hajiya already kin riga kin dauke ni aiki anan gidan ai, ko kora ta kika yi daga akin gidan?" Hajiya tace "ban kore ki ba kuma ba zan kore ki ba, ko baki san ana yin aiki biyu a lokaci daya ba? And also concerning aikin gidan nan, Dije tace min kusan komai ke kike 14 1:15 AM yi, maybe shi yasa har yanzu kika gagara yin kiba, daga yau na ware miki aikin ki, bedroom dina da nan falon su kadai ne naki. In kika yi kika gama sai ki tafi zaman shagon ki, in kin dawo da yamma sai ki dafa awarar ki, are you up to the task?" Safiya tayi shiru dan bata gane karshen ba, Hajiya ta maimaita mata "zaki iya yin hakan?" Da sauri ta gyada kai "zan iya Hajiya, sosai ma". And that was how it began. Ana bude shagon Safiya ta fara aikin zaman shago, kullum da assuba tana tashi zata hau saman Hajiya, dama kuma Hajiya ba'a dakin ta take kwana ba tana dakin Alhaji. Dan haka dakin nata bashi da datti gyaran sa babu wahala, cikin kankanin lokaci Safiya take gamawa sannan ta sauko ta gyara nata dakin tayi wanka ta shirya taci abinci ta debi na rana ta tafi shago. A can take wuni sai la'asar take dawowa gida sannan tazo ta dora dahuwar awarar ta. Ta kan dafa da yawa wani lokacin ta yi freezing sai take daukowa tana soyawa ana zuwa ana siya daga gida gida. Yadda take cinikin awarar har mamaki yake bata. Tana kuma diyar da danya, idan mutum yafi so ya soya da kansa a gida. Har a shago idan customers sunzo takan yi musu tallan awarar ta, daga baya sai ta fara soyawa tana tafiya da ita shagon ma tana siyarwa a can. Da lokacin albashi yayi Hajiya ta lissafa kudin albashin ta na aikin gida ta bata a hannunta, Sannan ta sake lissafa kudin albashin zaman shago ta sake bata, Sai ta tsaya tana kallon kudin kawai dan dai ita bata taba gain kudi masu yawan wadannan ba. A garin su ko masu aikin gwamnati jin suna daukan wanna kudin. Ta tashi ta je ta dauko kudin ribar awarar ta da take tarawa ta kara su akan albashin nata. And the first thing that came to her mind was wacce hanya zata bi ta juya wadannan kudaden su kawo mata wasu? Maman Maama [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Episode Thirty: Safiya Khalid Not Edited Kwana biyu bayan nan Adam ya dawo da duk takardun da zasu tabbatar da yarjejeniya, Hajiya still bata amince ba sai da ta dauki Safiya suka tafi a motar Adam din zuwa gurin lawyer din da yake gudanar musu da most legal services din su ita da Alhaji. Adam yana driving Safiya tana gefensa Hajiya tana baya sai ya fara yiwa Hajiya korafi. "Shekara nawa muna business da ke Hajiya, amma duk nuna wa kike yi kamar baki yarda da ni ba. Ni ma fa zan saka kudi na acikin harkar nan, wallahi in kika ji yawan kudin da zan saka sai kin yi mamaki, I only want to make sure cewa the whole 30% comes from me bana son wani ya shiga cikin maganar yayi hijacking komai daga gare ni shi yasa nake nema a cikin mutane na" Hajiya tana murmushi tace "na gaya maka ba kai ne ban yarda da kai ba, su ne ban yarda da su ba. Kuma idan da ace kudi na ne da bazan tayar da hankali na akai ba, but that girl sitting beside you is the most hardworking person da na taba gani a rayuwata. She went through a lot, more than abinda mutane da yawa zasu iya dauka a rayuwa. Ta sha wahalar rayuwa ba kadan ba, ta kuma sha wahala wajen gain ta tara wadannan kudaden da ta basu. Shekarar ta goma ko baccin kirki ba ta yi saboda ta cimma burinta, and I won't let her effort go to waste" yana kallon Safiya yace "I don't understand the ta sha wahala da kike fada, ba ta yi kama da wadanda suke cikin wahala ba, plus she is born rich ba irin mu da muka fara kasuwa from the scratch ba" Hajiya tace "oh, you are judging a book by it's cover. Wannan yarinyar da kake gani marainiya ce, babu uwa babu ba babu dangin uwa babu dangin uba, ko kuma in ce useless dangin uba, sanda ta shigo Abuja kayan da suke jikinta ma bata su aka yi ta saka ba nata bane ba. Ko kwandala bata da ita. And she worked and pulled herself up. Duk kudin da kaji ta ambata da bakinta cewa tana da su da gumin ta ta hada su". Ya dan yi slowing down yana kallon Safiya suka hada ido sai ta juya kanta tana kallon window. Yace "I thought yarki ce fa, ko niece haka" Hajiya ta gyada kai "yata ce a yanzu. She is the closest thing I have to a daughter" tun daga nan jikinsa yayi sanyi kuma ya fara thinking twice akan maganar. Suna yin packing a gaban office din lawyer din da zasu dauka ya juyo yana kallon Safiya "do you still want to go ahead with this ko kin chanja shawara?" Ta dan kirkiri murmushi, ta lura maganganun Hajiya sun sagar masa da guiwar sa sai tayi kokarin lightening up the atmosphere, tace "kar ka zama ragon maza mana Adamu, fargaba aka ce asarar namij" ya bude ido "wannan wanne irin sabo ne, Adamu fa kika ce, Adam sunana ba Adamu ba" tace "Adamu zan ce nikam. And remember I am your partner now dan haka you should get use to Adamu" yace "gaskiya ki samu ruwa a kusa ki kuskure bakin ki ki hada da istigfari, sunan Annabi guda kike bata wa, ko kin taba jin ance annabi Adamu?". Hajiya da take baya tace "kunga, ni ina da abinyi, ku taho muje muyi sauri mu gama abinda ya kawo mu. A office din lawyer din aka sake maimaita bayanai ya karbi katardun da Adam yayi drafting ya yi modifying using legal terminologies kowa ya amine sannan aka saka hannu. Da aka zo rubuta suna ne Safiya ta fadi sunan ta "Safiya Haladu" Adam ya yi dariya ta tsaya tana kallon sa tana tunanin menene abin dariyar, yace "no wonder! Yanzu na gane dalilin da yasa kika ce min Adamu. Ashe ashe bakin ne ya riga ya saba" ta bata rai "sunan baban nawa kake yiwa dariya?" Ya girgiza kai "ke nake yiwa dariya da baki iya fada dai dai ba. Khalid ake cewa ba Haladu ba", Ta juya tana kallon lawyer "kaga rabu dashi, dan na ce masa Adamu shine yake ramawa. Rubuta min sunana ka bani in saka hannu" lawyer yace "amma fa nima ina goyon bayansa. This is a new beginning, a new life, it warrants a new name" ta girgiza kai " have been using Haladu all my wife, credentials dina duk haka ne a jiki, I cannot change it for this only, in na chanja sunan I have no evidence to claim cewa nice" lawyer ya gyara zama yana kallon ta proudly yace "daga dukkan alama kin manta a office din wanda kike. 6 3 9:04 PM I can do all that for you in kina so" ta juya ta kalli Hajiya alamar shawara, Hajiya tayi mata murmushi tace "Safiya Khalid suits you more, kuma it is still his name" ta juya ta kalli lawyer din tace "ubuta" sannan ta kalli Adam da yayi sauri yace "yes!" Tace "ba dan ka fada bane ba fa, dan Hajiya ta fada ne. And you are still Adamu". A cikin sati biyu komai ya kammala. Aka gama duk cike ciken da za'a yi Adam da Safiya suka hada kudi jointly suka sayi 30% share na kamfanin mining and processing of gold wanda a lokacin ko official suna bashi da shi. And with their share kamfanin suka sami permit din da suke bukata dan fara operating a Nigeria. But sun gayawa Adam dama cewa it will be a long journey kafin komai ya daidaita. Yanzu babu abinda Adam da Safiya zasu yi sai dai su jira, su kuma cigaba da addu'a. Wannan contract din was what firstly brought them together, amma kuma ita din kawai agent ce da Allah ya aiko gare su, for they are meant to be together. Tun daga ranar da Safiya ta shiga falo ta ga Adam a gaban Hajiya, tun daga ranar rayuwar ta ta kuma taking another turn. Bayan turn din tattara kudin ta da tayi ta bashi blindly, sai kuma turn din yadda shi kuma ya makale mata kamar cingam. Da farko ta dauka he is just after the money, so yake a gama hidimar signing contracts din and he will go back to his life ya barta sai kuma in wani abin ya sake tasowa da yake bukatar ta a matsayin ta na partner din shi. But she was wrong. Tarkon da bata san sanda ta dana shi ba ya riga ya kama Adam, and he wasn't even trying to escape, he was comfortable and even glad cewa tarkon ya kama shi. And ga mamakin ta bata ji repulsion din6da takan ji ba a duk sanda wani namiji ya gwada irin abinda Adam yake gwadawa yanzu a kanta. She was glad that tarkon na ta ya kama shi. Gidan Hajiya ya zama gidan zuwan Adam, Abuja ta zama gurin zamansa duk kuwa da cewa most of his businesses a Kano suke. Kullum in yaje gidan sai ya fara kame kamen yazo zai kara yi mata bayani ne akan yarjejeniyar da suka kulla, in yana fadawa Hajiya haka sai kawai tayi ta nodding kai tana jin sa, in ya gama tace "haka fa" daga baya dai ranar nan da yazo yana ta yi mata dogon bayani da ta bashi wani bombastic side eye sai yaja bakin sa yayi shiru mid sentence, amma kuma fuskarsa dauke da murmushi dan ya fahimci ta gane inda ya dosa, tace "Please Adam spare me da wannan dogon bayanin, idan kazo gurin Safiya l am sure you have her phone number, call her kuje can akwai gurin da yamma tan gidan suke saukar samarin su ku zauna a can. Spare me please" yana cigaba da murmushi yace "okay, to bara in kira ta" sai ya tashi ya fita waje. An jima kadan sai gata nan itama ta fito, ta zauna a gaban Hajiya tana lissafa yatsun hannunta "Hajiya dama,...... . Adamu ne yazo…………yace wai akwai wata takarda..... Hajiya ta nuna mata waje "tashi kije yana waje yana jiranki. Wai ni yaran nan me suka mayar da ni ne? Yarinya karama suke son mayar da ni ko me?" Sa'adatu da tun shigowar Adam take kwance akan kujera tana danna wayarta ya juyo tana yiwa Safiya dariya tace "business partner din ne yazo? To manyan yan kasuwa maza aje a cigaba da tattaunawa akan business" Safiya ta harare ta ta fita tana murmushi. A gaban motarsa ta same shi a tsaye, ya taho shima suka hadu a hanya yace "ina yake?" Tace "me?" Yace "zobo na" tace "yau ba zobo zan baka ba, yau konon aya nayi maka mai dankaren dadi, amma sai ka kawo kudi" ta fada tana mika masa hannunta da yasha zanen lalle. Ya fara laluba aljihun sa sai kuma yayi ajjiyar zuciya "a bani bashi. Zan biya" ta bata fuska "ni bana bada bashi, amma tunda dai sunan ka Adamu zan baka, amma sai ka rubuta sunan ka ka saka hannu ka kuma rubuta ranar da zaka biya" yace "ko na rantse zan biva ma ba za'a bani ba? I promise you zan biya ki. Wata rana. Ke dai ki jira kawai ki gani". 5 1 9:04 PM Watanni suka wuce. Safiya bata yi folding arms dinta tana jiran maganar kamfani ta tabbata ba, ta cigaba da managing sauran 30% na kudin ta da Hajiya ta tabbatar bata zuba all her eggs in one basket ba. Ta cigaba da zaman shago, ta cigaba da hustling musamman yanzu ba bata Zuwa makaranta tana da all the 24 hours to herself. Sannan kuma gashi yanzu tana samun shawarwari da kuma ideas daga gurin Adam. And sometimes manly taimako. Yanzu indai yana gari yana taimaka mata da shiga kasuwa da sauran guraren da yake ganin are too risky for her. Wasa wasa soyayya mai karfi ta kullu a tsakanin su. Kamar yadda safiya bata taba yiwa kowa karya akan asalin ta ba haka shima Adamu bata yi masa karya ba, cikin lokaci kankani ya san komai a kanta, labarin Baba Hadiza kuwa sai da ya bawa wani dan duk zuwan da zaiyi sai ta bashi kuma duk wayar da zasu yi sai ta ambace ta, Abinda ya kara karfin soyayyar su kuma shine fashion da suke da shi iri daya, fashion for business, Yes, suna soyayya amma mostly hirar su ta harkar business ce suna sharing ideas suna bawa juna shawara. Zuwa lokacin ita ma ta san abubuwa da yawa akan sa. Ta san dan kano ne shi kuma he started his business from the scratch. Ba wai haihuwar sa aka yi into the money ba. A yadda yake gaya mata abinda ya fara siyarwa a duniya shine rake, rake ya fara siyarwa a layin su tun yana dan primary school, daga wanna sana'ar ya koma waccan daga waccan ya koma waccan har wani abokin babansa ya dauke shi jiran shago a kasuwar sabon gari. And that was where his gold business started. Shi wanda yake jire wa shagon sarkokin gold yake siyarwa, a hankali ya fara koyan business din shima, kuma yayi sa'a ubangidan nasa bashi da son bakin hali and he showed him the way har shima ya samu nasa jarin ya fara. Farko a cikin dan akwati yake zuba sarkokin sa yana yawo dasu yana siyarwa, daga baya ya fara samun connections da matan manya yana kai musu har gida suna siya, gari gari babu inda baya zuwa, gidajen yan siyasa da duk masu kwandala ya sani kuma he talked his way into the houses ya kuma siyar musu da kaya. A haka ya samu fada sosai a tsakanin manyan da yake business da su, a haka ya bude nasa shagon ya saka kaninsa Ahmad a ciki shi kuma ya cigaba da yawo gari gari, daga baya yawon nasa ya koma kasa kasa, he opened his next shop in Kaduna, wanda yana daga cikin abubuwan da ya siyar to get the contact, and another one in Abuja, Shagon da Hajiya tayi wa Safiya bargaining a bata partnership a ciki. Sai dai a yanzu Safiya bara san inda zata samu kudin da zata saka a cikin shagon ba. Adam bai yi karatu mai zurfi ba amma yana da gogewa sosai saboda yawn muamala da yake yi da mutane. Ya iya mu'amala da mutane. Kuma Safiya ta fahimci cewa he is very smart, principled and trustworthy. Yana da gaskiya sosai. And she felt safe with him. Sai dai kuma watanni bayan haduwar su he stated growing impatient akan maganar kudaden su da suka bawa kamfanin da ko takamaiman suna bashi ba shi. "'Safiya tsoro na ke ji. What if Hajiya ta fi mu gaskiya? What if suka gudu da kudin mu? Yaya zanyi kenan?" Safiya tayi dariya "then we will work and get another money. Kudi ne fa ba wani abu ba" yana girgiza kai yace "kudi kuwa sune wani abu. Kin manta duk wahalar da kika sha kafin ki same su? Ji nake da kanki kike bani labarin yadda kike dashi tun kafin asuba ba kuma zaki koma bacci ba sai dare yay nisa?" Tayi ajjiyar zuciya tace "ka san me? Da gaske naso yin kudi, but I never thought zan yi din, Actually, a ranar da Sauda ta rasu I never thought zan sake kwana a duniya. Daga nan kuma sai na koma tunanin ba zan kai shekara ba, and now shekara goma kenan har da watanni da mutuwar Sauda and I am still alive. Duk a cikin wadannan shekarun I was just living kamar a mafarki. Har yanzu ji nake kamar zan iya farkawa at any moment in tarar cewa mafarki nake yi ashe. I am living a far better life than I have ever imagined. So for me, I am just waiting for the death to catch up with me" yayi sauri yace "kowa ma a duniya haka ne. Duk ita muke jira. ) 2 9:04 PM So ke kina so ki ce min baki da wani plan for the future? What were you aiming at sanda kika fara sana'a?" Tayi shiru tana kallon bango, deep into her thoughts, sannan tace "Ina da dream for a future. A future were I will have a legacy, a legacy in form of kids, princes and princesses that I will raise with love and protect with my life. A cikin wannan mafarkin my kids will lake for nothing, they will never know fear, they will never know loneliness, and they will never know poverty. Ina so in haifi yaya, lots and lots of yaya" Adam yayi gyaran murya, ta juyo tana kallon sa sai kuma taji kunyar cewa tana maganar haihuwa a gaban sa, ta rufe fuskarta da hannunta, yayi murmushi "yanzu dai kina nufin in kara zage damtse kenan gurin neman dukiyar da zan kula da ke da wadannan princes and princesses din da za' a haifa min" ta bude fuskar ta tace "don't worry, we will take care of them together" ya girgiza kai "no. Idan muka yi aure kina da damar neman all the halal money that you can get, but it will be my duty to take care of you and all the kids we will have" Wasa wasa magana tayi karfi tsakanin Adam da Safiya, har ya fara maganar taking their relationship to the next level, ma'ana aure. Sa'adatu Safiya ta tura ta gaya wa Hajiya, Hajiya ta nuna jin dadin ta sosai dan dama tun sa da ta gane abinda yake tsakanin su taji dadin hakan dan tasan Adam mutum ne mai hankali da nutsuwa da kuma kokarin neman na kansa. Ta fahimci sun matukar dacewa shi da Safiya. Aka bawa Adam damar a turo kuma ya turo din, sai dai bayan maganar da mahaifansa suka yi da Alhaji sai suka nuna cewa suna son zuwa suga asalin dangin Safiya. Anan ne kuma rigimar ta tashi, dan ana gaya wa Safiya abinda suka ce tace ta fasa auren. Wannan ba karamin daga hankalin Adam yayi ba. Babu shiri ya baro Kano ya taho Abuja. "Safiya dan Allah. Kawai so suke yi suje suri tracing asalin ki shikenan. Ba wai acan za'a nemi auren ba, Alhaji zai iya bamu auren, amma Baba ya dage sai an je can tukunna" tace "saboda me?" Yace "saboda gaba. Aure zamuyi, Zuri'a muke da burin samu. Dole zasu bukaci sanin asalin mahaifiyarsu" ta girgiza kanta da sauri "idan ka gan i a garin nan to gawa ta aka kai. Idan ka ga yayana a garin nan to bana duniya. And ko bana duniya I want you to promise me ko hanyar garin ba zasu bi ba". Yace "ba zasu je ba in ba kya so. Ke ma kuma ba zaki je ba tunda ba kya so. Su Baba zasu je amma. I just don't want them to go ba tare da na gaya miki ba shi yasa na gaya miki din. Kin amince su je din?" Tayi shiru tana kallon sa, wata zuciyar tana gaya mata ta hakura da shi gabaki daya, wata zuciyar tana gaya mata ta hakura da auren ma gabakidaya. But when she opened her mouth she heard herself saying "idan nace kar su je zasu bari ayi auren ba tare da sunje din ba?" Ya girgiza kai "I am afraid no" And love over powered Safiya's hatred for her family, she let them go. Hajiya ce ta yi magana da Hajiya Kyauta, ita kuma while still insisting bata son a san ita ta dauki Safiya, ta basu address din gidan baban Safiya a garin Kura da kuma gidan kanin baban ta., Suka je har can din suka yi tambayoyin da suke bukata suka tabbatar da kasancewar ta yar garin kuma yar Alhaj Haladu sannan suka dawo suka cigaba da neman aurenta a gurin Alhaji Nasiru, A hankali hidima ta kankama, aka kawo duk abubuwan al'ada dai da gwargwado aka saka rana aka gama komai. Adam ya samu gida ya kama musu rent anan Abuja dan baya son ya rabata da kasuwancin ta, shima kuma yanzu yafi mayar da hankali akan shagon sa na nan Abuja, na kanon mostly kaninsa Ahmad ne yake handling. Suma kuma su Hajiya Maryama da Alhaji Nasir sunyi namijin kokari wajen zubawa Safiya kayan daki na fitar kunya, yayin da Sa'adatu ta shiga ta fita ta tabbatar cewa bikin ya tsaru ya zama very unique and classy babu wanda zai kushe sai dai idan hassada ce yake yi. 3 2 9:04 PM Safiya ta so ta fitar da kudi ta yiwa kanta gata, amma Hajiya Maryama tace babu abinda zata yi wa kanta "wannan auren da zamuyi miki shine last gatan da zamuyi miki, daga wannan karon kin bar hannun mu kuma bama fatan ki dawo. Kin koma hannun mijin ki, amma still ina son ki sani cewa muna nan anan gidan babu inda zamuje a duk sanda kike bukatar wani abu ko wata sharawa ki zo muna maraba lale da ke". Safiya tamkar ya take a gurin Hajiya Maryama. In har ba maganar kuka taba yi da ita ba ba zaka san ba uta ta haife ta ba. Duk wasu harkokin ta ita take dorawa akai. Duk inda zata je da ita take zuwa. Ranar nan ma da zata je gidan ambassador Muhammad Dikko, da ita taje, Anan gidan Alhaji Nasiru aka daura auren Safiya, shine waliyyin ta. Da dare kuma aka kai Safiya gidan mijinta. A lokacin tana da shekaru ashirin da biyar a duniya, A ranar Safiya tayi kukan da rabon da tayi irinsa tun kafin zuwan ta Abuja. Kukan rabuwa da Hajiya da kuma Sa'adatu, ta yiwa Hajiya Safiya ta so ta fitar da kudi ta yiwa kanta gata, amma Hajiya Maryama tace babu abinda zata vi wa kanta "wannan auren da zamuyi miki shine last gatan da zamuyi miki, daga wanna karon kin bar hannun mu kuma bama fatan ki dawo. Kin koma hannun mijin ki, amma still ina son ki sani cewa muna nan anan gidan babu inda zamuje a duk sanda kike bukatar wani abu ko wata sharawa ki zo muna maraba lale da ke". Safiya tamkar ya take a gurin Hajiya Maryama. In har ba maganar kuka taba yi da ita ba ba zaka san ba uta ta haife ta ba. Duk wasu harkokin ta ita take dorawa akai. Duk inda zata je da ita take zuwa. Ranar nan ma da zata je gidan ambassador Muhammad Dikko, da ita taje. Anan gidan Alhaji Nasir aka daura auren Safiya, shine waliyyin ta. Da dare kuma aka kai Safiya gidan mijinta. A lokacin tana da shekaru ashirin da biyar a duniya. A ranar Safiya tayi kukan da rabon da tai irinsa tun kafin zuwan ta Abuja. Kukan rabuwa da Hajiya da kuma Sa'adatu, ta yiwa Hajiya kuma adduoin da sai da suka saka ita kanta hajiyan kuka tare da duk wanda yake gurin, A haka Hajiya ta rungume ta ta kaita dakin mijinta tana matukar jin dadi a ranta, ita ta san Safiya a gurin ta investment ce, investment din da ba a duniya zata samu ribar sa ba, a lahira ne,[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: A big sorry to those that waited for Safiyya yesterday owner A big thanks to those that checked up on me Some things cannot be explained. 21 6:49 AM Safiyya Episode Thirty One: The Legend Safiya became very emotional tun da aka kaita gidan miji, tun daga kukan rabuwa da Hajiya kuma shikenan sai ta zarce kullum kuka ta bar ango da aikin rarrashi, amma shi ya fahimci zuwa lokacin ba wai auren take yiwa kukan ba ko kuma rabuwa da Hajiya ba, loneliness ne yake damunta, tana missing din familyn ta sosai. Ta koma kullum sai ta yi hirar su, kuma da ta fara sai hawaye, Adam ya fahimci abin nata har da survivors guilt, a zuciyarta tana feeling guilt na cewa su sun mutu ita kuma tana raye, and she is living the life that idan da ace suna raye ba lallai ne ta samu wannan rayuwar ba. One week after the wedding ya tashi da safe ya neme ta a dakin su ya rasa, yayi ta zagaya gidan yana neman ta sai can ya samo ta a backyard dinsu tana zaune a kasa ita kadai tana kallon flowers din gurin, ya je ya zauna a kusa da ita ba tare da yace mata komai ba. Sun jima a haka sannan ta juyo tana kallon sa da idanunta da suka kumbura saboda kuka tace "da kai aka je Kura ko su Baba ne suka je su kadai?" Yace "da ni aka je" ta juya ta cigaba da kallon flowers din sannan a hankali tace "ina so zan je. In ka yarda". Ya saka hannu ya jawo ta kan kafadarsa sannan ya zagaye ta da hannunsa guda daya yace "of cause we will go in kina son zuwa, just tell me yaushe kike so muje" ta kara kwanciya a jikinsa tace "jibi" suka saka yin shiru zuwa wani lokaci sannan yace "I saw the rooms, na ga dakunan da suka fadi. Kasar tana nan har yanzu" tace "I want to see it". Kwana biyu bayan nan suka dauki hanyar Zamfara da sassafe, dan tun kafin asuba tayi suka fita sai a hanya suka tsaya suka vi sallah. Su kadai kuma babu wanda suka gaya wa. The drive was joyous as well as emotional for Safiya saboda tana jin dadin companion dinta amma kuma tafiyar tana tuna mata tahowar da tayi zuwa Abuja over 11years ago, a hanya hirar da kawai take bashi, ranar har da hirar Baba and the little she can remember about him musamman irin soyayyar da ya nuna mata ita da yan'uwan ta. They talked about yadda irin auren Alhaji Haladu da Baba Hadiza yake random a cikin al'ummar mu da kuma yadda irin auren yake affecting zumunci a tsakanin yan gida daya. It is halal tabbas, amma wata halal din ana barin ta ko dan kunya da abinda zata haifar nan gaba. Wani ma sai yayi retire, da kudin gratuity dinsa zsi je ya auro yar karamar yarinya ta zo kuma ta fara haihuwa bayan sun gama girma matansa kuma sun manyanta, sai kuma yazo ya biye mata yayi ta yarinta yana bakanta ran matansa da yayansa, wannan kuma sai ya kara hura wutar kiyayyar amaryar da kuma yayanta a zuciyar wadancan. A karshe ya mutu ya bar baya da kura. Su kuma yayan da aka haifa basu da laifi, amma a karshe sune suke paying price din abinda ba su suka siya ba. Karfe 10 na safe a Gusau tayi musu, anan suka tsaya suka samu wani eatery suka ci abinci sannan suka dauki hanyar Kura. Few minutes after that suna garin Kura, Tun da suka shiga yayi slowing down yana tafiya a hankali ita kuma tayi shiru tana karewa garin kallo, nothing much has changed tun barinta garin, except for few houses da taga an gina an ld wadansu an sake musu fasali zuwa na zamani amma babu wani major change a garin, dan haka tar take gane hanya tiryan tiryan har kofar gidan su. Abinda ta fara gani shine tarin kasar da ta kasance ita ce dakin da tayi spending most of her childhood in. She could still feel the moist, dark and suffocating nature of the rooms, their laughter together ita da kannnenta da Baba Hadiza, sheshshekar kukan su idan suna cikin bakin ciki, ta rufe idonta tana tuno sound din kukan Khadijah sanda bata da lafiya "Baba Hadiza ki kaini asibiti bani da lafiya". Ta bude idonta tana jin echo din hun Sauda a lokacin da mota ta kade Baba Hadiza. Ta juya da sauri ta kalli gurin, a idonta tana gain gizon sanda motar ta daki Baba Hadiza ta tashi sama sannan ta fado kan kwalta. Ta tuna da yadda jini ya ringa fita daga kan ta, yadda jinin ya jika ta ita da Sauda. Ta bude tafin hannun ta tana kallo, kamar mai kokarin gain jinin a jikin hannun. Adam ya saka hannun sa cikin nata yana kallon yadda hawaye yake bin fuskarta yace "kina so mu koma?" Ta girgiza kan ta "no" sai ta cire hannun ta daga cikin nasa ta bude kofar ta fita. Sai a lokacin ta lura da cewa mutanen unguwar kusan kowa da yake gurin a lokacin motar ta su yake kalla, irin anga bakuwar mota ta tsaya kuma ba'a san waye a cikin ta ba. Ta juya tana kallon inda suke suyar awarar su ita da Sauda, a kofar gidan makota, saboda basu isa su yi a kofar gidan su ba. Ta taka a hankali zuwa kofar gidan ta shiga soron, yana nan shima yadda ta sam shi sai dai ya kara lalacewa, katangar duk ta tsatstsage, rufin ya taho zai fadi sai itace aka saka aka tokare shi. Langa langar da aka saka aka raba soron gida biyu babu ita, haka jakankunan kayan su da ta bari a wajan babu su suma. Daga dukkan alama soron ma ba'a amfani da shi yanzu dan dakunan su da suka fada kuma ba'a gyara ba sun saka gidan ya zama bashi da takamaiman mashiga. Ta shiga tsakar gida tana bin gidan da kallo, daga dakin da yake farko, dakin da nan ne inda yake na Baba Hadiza sanda Alhaji Haladu yana da rai, dakin da a ciki aka haife ta taga wata mata da bata sani ba ta fito ta a kallon ta "'baiwar Allah lafiya? Daga ina?" Bata amsa mata ba ta cigaba da bin gidan da kallo. Babban abinda ya ja hankalin ta a chanjawar da gidan yayi shine bedroom din Inna Sa'ade da taga ya rushe shima. Sabon dakin da aka yi mata ginin bulon siminti aka jingina shi a jikin nasu na kasa har yayi sanadiyar lalacewar nasun kuma yayi sanadiyyar rayuwar Sauda, shima ya fadi, kuma daga alama ya jima shima da faduwar, amma kuma kamar nasu shima ba"a gyara gurin ba yana nan a bude, sai ginin kasa da aka yi aka toshe kofar tsakanin cikin dakin nata da falon ta. Safiya ta wuce matar da har yanzu take yi mata magana ta doshi kofar falon Inna Sa'aden, kafin ta daga labule taji murya a bayan ta, muryar yayanta Dauda "ke wacece ne wai ana ta yi miki magana kinyi wa mutane shiru?" Ta juyo da sauri ta sauke rinannun idanun ta akan sa, ya ja da baya kadan kamar wanda yayi gamo, "Baba Hadiza?" Ya fada, sai kuma ya chanja "Safiya?" Bata amsa masa ba sai ido da take binsa da shi. Muryar sa tana nan yadda take bata manta ta ba, ta tuno sanda yace "ina uwar ta ku? Ko bata dawo daga yawon karuwancin ba?" Amma kuma kamannin sa gabaki daya sun chanja, ya rame ya sirance yayi baki, kana ganin sa ka ga wanda shaye shaye yayi wa kamun mutu ka raba. "Lantana! Lami!" Ya fara kwalla kiran sunan yayyen su wadanda suke yaya ne a gurin Inna Gaje. Lami ta fito daga dakin Inna gaje da sauri tana gyara daurin zani. "Kai lafiya kake min irin wannan kiran mafarautan? Ba dai zan baka rancen wani kudin ba dan. . ...." Sai kuma ta tsaya tana kallon Safiya. "Safiya" ta kira ta direct "Safiya ke ce haka? Ke ce a gidan nan?" Safiya ta tuno ta sanda take zazzagin Baba Hadiza tana kuma kokarin dukan ta a dai dai lokacin da aka dauki gawar Alhaji Haladu. Ta kuma tuno ta sanda suke yi musu watsi da kaya a waje suna cewa sai sun bar musu gida, Baba Hadiza tana ta kuka tana bin su tana rokon su. Ta juyo sosai tana kallon ta ta kira sunan ta ita ma "Lami" duk kuwa da cewa Lamin da haife ta dan tana da yaya sa'annin ta. Sai kuwa Lami ta rafka salati "jama'a ku fito. Safiya ce a gidan nan jama'a. Ashe tana raye. Jama'a ku fito ku ganta dan in tabbatar ba gamo nayi ba" Dauda yace "gani nima ina ganin ta kuwa? Wanne irin gamo? Zamuyi gamo ni mu biyu?" Ta watsa masa kallon banza "kai dalla can, kai me idon ka yake gani in banda kwaya? Ina kiran mutane masu hankali ne su zo su taya ni gani" nan take sai masifa ta kaure a tsakanin su. Safiya ta wuce su ta shiga dakin da take ta hari tun da ta shigo gidan. Sai dai tun da ta daga labule taji dakin yana wari, wani wari kamar warin mushe. Ga duhu tamkar dakin su na da saboda tagogin dakin duk a rufe suke. Sai da ta dan jima a tsaye a gurin sannan idon ta ya washe, a lokacin ne ta ga mutum a kwance a kan katifa a tsakar daki. 14 6 3 6:52 AM Sama sama take jin murya tana kiran sunan ta "Safiya? Safiya ke ce? Safiya" ta durkusa a gaban halittar da take kwance a gabanta tana kallon ta. Ta rame ta motse ta yamushe, Inna Sa'ade ce. Kafafuwanta duk guda biyun babu su an yanke su. Daga jikin ta da kuma katifar da take kwance a kai ne warin yake fitowa. Sai dai bakin ta yana nan tas, kuma daga dukkan alamu tana cikin hayyacin ta. "Safiya daki na ne ya fado min ina kwance ina bacci, kafafuwana duk duka kakkarye sai da aka yanke su, Balarabe yayi hatsarin mota ya mutu, sauran yaya na duk sun gaji da kulawa da ni suna can gurin matayen su, Sai Dauda shi kuma babu abinda yake sai shaye shaye, komai nawa ya sace ya siyar ya sayi kayan shaye shayen sa.. ..." Ta cigaba da magana non stop, kamar neman wanda zata yiwa magana da ma take yi, kamar ta jima ba ta yi magana da kowa ba. Safiya ta mike tsaye ba tare da ta ce mata komai ba ta doshi kofa. Sai da taje bakin kofa sannan inna Sa'ade ta sake kiran sunan ta "safiya"Safiya ta dakata sannan ta juyo tana kallon ta, tace "ki godewa Allah da Sauda mutuwa tayi ba ta zama iri na ba. A wani lokaci mutuwa rahama ce, ni yanzu neman ta nake yi taki zuwa". Har ta koma tsakar gida ana cigaba da rigima tsakanin Lami da Dauda. Ta wuce su again ba tare da tace komai ba ta shiga dakin Inna Gaje. Tana zaune akan tabarma ita kadai tana ta maganganu kasa kasa, har Safiya taje gabanta ta durkusa bata san ta je ba, kuma Safiyan bata gane me take cewa ba. Maganganu kawai take yi marasa ma'ana. Ga tsufa ita ma ta koma kamar tsumma. "Da yazo ya dauki kazar sai suka tafi cikin ruwan sama, kuma saniyar bata da ilimi, Allah dai ya tona asirin takalmi, Amen Ameen" Safiya ta mike tsaye tana cigaba da kallon ta sannan ta saka hannu biyu ta share hawayen fuskarta ta juya ta bar dakin. Tana fita Lami ta sske kokarin tarar gabanta, ta lura yayan lamin suna zagaye da ita, da alama zawarci take yi. "Safiya ina kika je tsahon shekarun nan. Munyi ta neman ki bamu same ki ba. Mun dauka ma ba kya duniya" Dauda yace "ina taje kuwa in banda yawon duniya, namiji ne fa yanzu ya kawo ta a katuwar mota, a ina Safiya zata samu shiga irin waccan motar in dai ba yawon duniya take yi ba?" Lami tace "dalla yi mana shiru, ka kalle ta mana ka gani? Ko dan shaye shaye ya toshe kwakwalwar ka. Bata yi kama da abinda kake fada ba, kama take yi da matan masu kudi. Ka sani ko mijinta ne? Ko aure ta yi? Safiya kiyi min magana mana ina ta yi miki magana". Still Safiya bata ce komai ba, ta wuce ta tsakiyar su taje ta hau ta kan kasar da shekaru suka saka ta zaizaye ta zama bata da yawa, ta fita daga gidan ta koma mota inda ta bar Adam. Yana tsaye a jikin motar yana kallon cikin gidan, daga dukkan alamu hankalin sa ba'a kwance yake ba, yana gain ta fito yayi ajiyar zuciya sannan ya bude mata kofa ta shiga ta zauna a dai dai lokacin da yaya Malam ya kawo kai yana kokarin shiga gidan, ya tsaya yana kallon motar daga alama bai gane wacce ta shiga cikin motar ba, Safiya ta bishi da kallo, yana nan kamar yadda ta san shi, ssi dai shekaru da suka karu akan na da, sai kuma shekarun suka saka taga yayi mata kama da baban su. Ta rufe ido tana kokarin tuno wa da fuskar Baba, suna kama sosai da yaya Malam, ta bude idon tace da Adam, "Drive, please" ya taka motar a dai dai lokacin da yaya Malam ya gane ta yace "Safiya?" Amma bata amsa masa ba kamar yadda bata amsawa kowa a gidan ba. Gidan Hajiya Kyauta tayi masa kwatance suka je, Hajiya Kyauta tayi murnar ganin su sosai dan dama bata samu zuwa bikin nasu ba saboda bata jin dadi sosai. Suka zauna suka yi hira da ita sannan suka ci abinci. A lokacin ne take bawa Safiya labaran abubuwan da suka faru a gidan su, yayan ta Balarabe wanda Inna Sa'ade take ji da shi a cikin yayanta ya mutu, ita kuma kasar da ta kashe Sauda ita ce ta lalata nata ginin na zamani sannan babu zato babu tsammani dakin ya fado mata ita ma cikin dare, abinda yayi sanadiyyar kafafuwanta biyu duk sai da aka yanke su. 15 8 4 6:52 AM Ita dama bata da yaya mata, yaya mazan suka fara jinyarta kamar gaske daga baya duk kowa ya kama gabansa sai Dauda da yayi aure yanzu yake zaune a asalin dakin Baba Hadiza. Su sauran yayan daudan suke aikowa kudi wai ya kula da mahaifiyar ta su, shi kuma sai ya cinve kudin. Hatta fitsari da bahaya a lokuta da dama sai dai tayi su a kwance. Inna Gaje on the other hand tsufa yazo mata da tabin kwakwalwa, kanta ya kwace bata gane kowa bata gane komai. Lami da lantana duk suna gida suna zawarci. Anan Safiya ta gaya wa Hajiya Kyauta abinda yake ran ta. "Hajiya Kyauta ina son siyan gidan mu idan zan samu. Ina son ki samo min wanda zai siya da sunana dan ba lallai su siyar ba idan suka ji ni zan siya" Hajiya Kyauta tace akwai dan ta zai iya. Safiya ta cigaba "so nake ya bisu daya bayan daya yayi musu tayin siyan gidan, tunda gidan gado ne nasan da yawa zasu siyar, ina da takardun bangaren mu har yanzu a hannuna, idan da zan samu ko da rabin cikin ne sai in hada da inda muke da shi ina son gina wa Baba Hadiza masallaci a wajen. In kuma sunki siyarwa sai a samu wani filin daban a siya ayi ginin" Hajiya Kyauta tace "zasu siyar ma, Gabaki dayan su fa a kone suke talauci yayi musu katutu, babu wanda za'a yi masa tayin kudi yaki karba, Wadanda kawai suke cikin gidan sune babu tabbas din zasu siyar, amma kuma sauran sunfi su yawa". Bayan sun ci abinci sunyi sallah anan gidan sai suka dauki hanya suka koma Abuja. Zuwan su Kura ya taimaka wa Safiya sosai gurin samun composure da ajiye past dinta a gefe ta kuma fuskanci future. Cikin dan kankanin lokaci cinikin gidan su ya kammala, kuma kamar yadda Hajiya Kyauta tayi predicting haka ne ya kasance, kusan kowa a gidan ya siyar da kason sa, hatta Dauda ya siyar da nasa da kuma na Inna Sa'ade, yayan Inna Gaje ma sun ce a siyar da nata a basu kudin, Lami da Lantana ne kadai su ka bijire dan basu da gurin zama, sai Safiya tace a kara musu kudin yadda zai ishesu su sami gurin zama, bata son shiga hakkin kowa ba kuma ta son takurawa kowa. Ganin cewa in sunki siyarwa ma kason subbashi da yawan da zai ishe su su zauna a ciki sai suka hakura suka siyar suka nemi rent din wani gidan suka tafi da mahaifiyar su. Safiya kuma a bisa amincewar hakimin garin ta fara cika burin ta na gina katon masallacin da sunan mahaifiyarta a matsayin sadakatul jariya a gare ta. Gini aka tsara mai kyau irin na zamani, tun daga harabar masallacin har cikin sa abin sha'awa ne, Sai kuma Adam vavi furnishina masallacin va saka duk abinda ake bukata tun daga kan fankoki da mic da Alqur'anai da sauran littattafan addini har carpets, ya kuma yi borholes guda uku a zagaye da masallacin duk da sunan Baba Hadiza. Bayan an kammala komai sai suka danka masallacin a hannun Haruna dan Hajiya Kyauta saboda maintenance, suka ce duk abinda ya lalace ko kuma abinda ake bukata sabo a ciki ya kira ya fada musu. And then life goes on. Suka koma back to their various kasuwanci. Shekara guda bayan auren su Safiya ta bude awara joint a Abuja, tace ba zata bar sana'ar awara ba. A shekarar ne kuma suka yi handing over na shago da Hajiya, shagon ya dawo completely na Safiya ne. A karshen shekarar ne kuma kamfanin gold din da suka yi investing in ya gama kammala ya fara functioning, har zuwa lokacin dai bass samun komai daga gare shi amma kuma hankalin su ya kwanta tunda sun zama confirm share holders na kamfanin. Da shekara ta sake zagayowa ne aka fara basu profit, Safiya sai da ta girgiza da adadin kudin da ta gani a rubuce kuma wai nata ne ita kadai a matsayin riba kawai bayan jarin ta da still yake ciki. Adam ma yayi mamakin nasa, tun farko ya san cewa akwai alkhairi a cikin abin amma bai dauka zai kai haka ba. A take Safiya ta sake mayar da ribar ta cikin kamfanin ta kara girman share dinta, while Adam used his own profit ya siya musu gidan zama a Abuja. Dama ya gaji da biyan rent. 23 9 6:52 AM The house was huge and it was all Safiya have imagined as aljannar duniya. The first thing she did a gidan shine enlarging picture din su ita da Baba Hadiza da su Sauda ta kafe a babban falon gidan. Together, they furnished the house to their exotic taste. Babu ce kawai babu a cikin gidan. Sai kuma yaya. Tun bayan auren Safiya take saka ran ganin ciki amma shiru, duk wata sai tayi ta addu'a ta kuma yi ta sadaka amma a karshen watan ta sai taga period. Tun tana tura maganar to the back of her mind har ta fara fito da ita tana furtawa. And Adam kept saying lokaci ne bai yi ba that their princes and princesses are on their way, amma shiru basu karaso ba. Sai dukiya ce take zuwa. Her story and marketing strategies became a legend, Kullum cikin signing business contract take yi da different companies wasu neman shawara suke yi daga gare ta wasu aiki suka bata to market their products wasu kuma ambassador suka bata na brand dinsu. Wasa wasa duk kamfanin da ta fara hulda da su sai suga cigaba sai wasu kamfanin suma su fara neman ta. A shekaru uku na farkon auren Safiya tayi signing business contracts babu adadin, at a point, she even had to have her own lawyer da zai taimaka mata wajen tace contracts din kar taje tayi signing akan abinda yake illegal. A lokacin Safiya tafi Hajiya da Alhaji gabakidayan su kudi. Ranar nan ta dawo daga wani taro a gajiye, babu tunanin abinda take yi sai na zuwa gida ta samu tayi wanka ta kwanta ta yi dogon bacci. Sai dai tana tsayawa a bakin gate ta ga mutane a zaune a kasa dirshan, Allah ne kadai ya san dadewar su a gurin. Sai dai duk da gajiyar da take ciki da kuma rashin kyawun yanayin su, ta gane su. Yaya Malam ne da Lantana. Taji kamar ta saka reverse ta fita da motar a guje, amma kuma gidan ta ne wannan ba nasu ba, ita zata kore su ba su zasu kore ta ba. Sai dai babbar tambayar anan ita ce "ya akayi suka san gidan? Me kuma ya kawo su", Tayi kamar bata gansu ba ta danna horn. Mai gadi ya taso da sauri ya bude mata gate a lokacin da suma suka taso da sauri suka taho wajanta, yaya Malam kamar zai fadi. ta danna motar cikin gidan a guje, tana packing ta hango su suna rigima da mai gadi, yana kora su waje yana kokarin rufe gate su kuma suna kara cuso kai. Bata ce komai ba har sai da ya gama rufe gate din sannan ya taho inda take "Hajiya sannu da zuwa. Wadansu ne tun safe suka takurawa gidan nan, na rasa yadda zanyi dasu, babu irin zagi da tsoratarwar da bani musu ba sunki tafiya" ta bude kofa ta fito tana jin zuciyar ta tana zafi, mai gadin ya cigaba da magana "sunce su yayyen ki ne, wai daga Kura suke" ta juyo da sauri tana kallon sa tace "ka gaya musu na basu minti goma, ko su bar kofar gidan nan ko in saka a rufe min su, ka gaya musu nan Abuja ce ba Kura ba, in na rufe su babu mai fito da su har abada". Daga haka ta shige ciki ta rufe kofa. Sai dai baccin kasa yiyuwa yayi duk kuwa da wankan da tayi ta kuma kwanta a lallausan gadon ta. She have forgiven them, amma ta kasa manta irin abubuwan da suka yi musu da kiyayyar da suka nuna musu, bata fatan wata mu'amala ko da ta magana ne ta shiga tsakaninsu. Tana nan a kwance Adam ya dawo daga tasa hidimar, Ya tsaya a bakin kofar dakin ta yana kallon ta, yace "baccin yamma babu kyau" tayi juyi "yaki zuwa ma baccin, I am extremely tired" yace "I know. How did the meeting goes?" Tace "just like we expected, wai suna son in je musu taro ne a Beijing, kuma inyi magana a matsayin representative din su" yace "okay. Sai mu shirya zuwa china kenan" ta tashi zaune "I didn't say yes, nace sai nayi magana da kai first" yace "to ni na ce miki yes. It is a golden opportunity, zaki hadu da mutane da yawa a can. Kawai kiyi amfani da marketing strategies dink and win their hearts, daga nan zaki samu connections da zasu kaiki next level in life". Bata ce komai ba har ya karaso ya zauna a bakin gadon yana kallon ta. Sai yace "akwai baki a falon kasa" ta tashi tsaye da sauri, ta fahimci bakin da yake nufi "I will not see them" ta fada matter of factly" ya gyada kai "then I will see them. 24 6:52 AM Ba zan iya barin su a waje ba knowing jinin ki ne su, and they refuse to go, kuma sun taho tun daga Zamfara sannan basu san kowa a Abuja ba bai kamata mu ki ganin su ba". Ta sake maimaita wa "I will not see them. will have nothing to do with them" shima ya maimaita "then I will see them". Ya juya kuma ta mike ta fita daga dakin itama. A kan barandar da ta zagaye babban falon gidan, wadda kuma ita ce zata kai ka dakunan sa da nata, anan ta tsaya tana kallon bakin nasu a zaune a kasa suna ta kalle kalle, tana kallon yaya Malam ta tuno sanda mota ta kade Baba Hadiza yayi tafiyarsa ya barsu rungume da gawar ta, sai a lokacin ta lura har da bagkon kaya suka taho. Ta ga Adam ya bude dakunan da suke kasa sannan yazo guri su yace "tace ba zata gan ku ba, ta kuma ce in kuka sake dawowa zata dauki matakin shari"a a akan ku, amma nayi mata magana, ga dakuna nan ku shiga akwai duk abinda kuke bukata a ciki, za a kawo muku abinci, ku kwana anan, gobe zan bawa maigadi kudin mota ya baku ku koma inda kuka fito" Yaya Malam ya mike daga zaunen da yake a kasa ya koma kan kujera ya zauna yace "'wai kai in tambaye ka, uban waye ya daura muku aure da ita? Shin wai auren ma kuke vi o kuma zaman dadiro kuke yi? Saboda ni dai ban daura mata aure ba kuma kaf dangin mu babu wanda ya daura mata aure, Zan kai ku kotun shari'ar musulunci in yaso sai inga wanda zai daure wani tsakanin ni da ku". Maman Maama [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA❤️‍🩹 Episode Thirty Two: The Legacy Not Edited Safiya ta bar inda take ta sauko kasan da sauri kamar wadda ake hankada ta, tazo ta wuce su da sauri tana jin Adam yana cewa tunda ba da mutunci suka zo ba ya fasa basu dakin, ya juya yana rufe kofar dakin da ya bude, Lantana ta fara kokarin yiwa Safiya magana amma bata amsa mata ba ta fita waje, tana fita sai gata sun dawo tare da maigadi ta tsaya a tsakiyar falon tana bin su da kallo tana lura da yadda yaya Malam yake kokarin washe mata baki "gata nan ta dawo ma ai, kanwata ce, baban mu daya ni da ita" ta juya tana kallon mai gadin tace "anan kusa akwai irin matasan nan yan shaye shaye wadanda basa jin tsoron uban kowa?" Mai gadin ya fara fahimtar me take nufi yace "babu anan layin Hajiya, amma akwai anan layin bayan mu, neman su kike yi?" Tace "ka zagaya dan Allah da sauri ka samo min kamar guda biyar, ina son su zo su fitar min da wadannan daga cikin gidan nan ba ta hanyar mutunci ba, kai kuma ka gane fuskokin su, in na fita gobe zan sivo maka bindiga, duk wanda ya kuma dawowa a cikin su ka harbe shi a kata ni na saka ka", Mai gadin ya gyada kai da sauri "to shikenan Hajiya, bara in yi sauri in kirayo su, harbi kuma sai dai in ba'a bani bindiga ba, duk wanda aka kora yaki tafiya kam ai barawo ne...... ...." Ya fita yana cigaba da maganganun sa Safiya ta juya ta koma sama da sauri kamar yadda ta sauko da sauri. Yaya Malam ya kira sunan ta "Safiya..... Safiya yanzu ni zaki ce a kira wo wa yan shaye shaye suyi min korar kare daga gidan ki? Ni zaki ce a harba idan na kuma zuwa gidan ki? Uba daya ne fa ya haife mu ni da ke. Wa kike dashi a duniya da ya wuce mu. Mu kadai zaki gani ki kira da yan'uwa kaf duniya" ta dakata a saman stairs din ta juyo tana kallon su kamar zata yi magana, duk suka tsaya suna jiran abinda zata ce, sai kuma ta kuma juyawa ta hau kan baranda suka daina gain ta. Suka juya suka kalli juna "ato magana ma bamu isa tayi mana ba, wato bamu isa ma tayi musayar yawu da mu ba, lallai duniya mai abin mamaki, wai Safiya? Safiya dai yarinyar da in nazo gida take wankewa yaya na kashi take yi musu wanka idan sunci abinci sun rage su bata taci ita da kanwarta, wai ita ce yanzu take yi mana korar kare da ga gidan ta". Yaya Malam ya koma ya zauna akan kujera tare da yin tagumi da hannun sa "duniya kenan. Ance fa kudin da take da shi yafi dukkan tunanin mai tunani. Amma ruwa yarinyar nan ba zata bamu musha ba kenan take nufi?" Lantana taji an taba gate ta zabuwa "yaya ka tashi mu tafi, wanna yarinyar mai idanu a tsatstsaye wallahi in bamu bar gidan nan ba ba karamin wulakanci zata yi mana ba, ka ga fa ta tura a dauko mata yan daba. Ka tashi mu tafi" ta fada tana jan rigarsa" ya ture hannunta "mu tafi ina wai? Kina da kudin motar komawa gidan ne?" Tace "bani da shi amma zan nema a waje, wallahi ba zan zauna a nakasta ni a banza ba, wannan katon gidan ko kashe mu ta saka akayi tana da gurin da zata binne mu babu wanda zai sani. Kazo mu je ko gidan abokin na ka ne mu kwana a can" Ya mike yana kallon been da Safiya ta hau sannan yayi kwafa "zamu sake haduwa ne" Lantana tace "kai dai kazo mu tafi. Da mun sani mun lallaba mijin ta naga kamar ya fita saukin kai shi zamu iva samun wani abu a gurin sa, ko kuma ya lallaba mana ita ta saurare mu, amma yanzu kayi mana wasa da damar mu......... Suka fita suna cigaba da maganganu kasa kasa. Safiya ta bisu da kallo har suka bar falon sannan ta juya ta koma daki ta kwanta a kan gado tare da jan bargo ta rufa. Ta san babu wasu yan daba a unguwar, shima mai gadin ya san babu, kuma yadda suke din nan ko mai gadin shi kadai ta saka zai iya daukan su aka ya fitar da su daga gidan ballantana akwai sauran ma'aikatan gidan, amma tana so ne ta nuna musu how far she can go akan hana su shiga rayuwar ta. Kuma yanzu from maganganun su kadai ta san abin da ya kawo su, ba komai bane ba sai kudi, kuma ta rantse ta kuma rantsewa, kwandalar ta ba zasu ci ba. 23 A 00 3 10:03 PM Adam ya shigo dakin yana kallon ta, ya san idonta biyu, yace "naso ace da mutunci suka zo, da ko kudin mota sun samu. Now they are stranded in Abuja basu da ko kudin da zasu koma gida" ta mike zaune tana kallon sa tace "da in basu kudi na gwara na bude window na watsa kudin waje, watakila almajirai su dauka suyi amfani da shi. They are after my money, my hard earned money, kuma wallahi kwandala ta ba zan basu ba". Adam ya zauna a bakin gadon ya rike hannunta yace "wannan shine Zuwan su na farko gidan nan, ina so ki fahimta kuma ki saka a ranki cewa it won't be the last, they will come back. Kudi suke so kuma na yarda da ke idan kika basu they will want more and more kuma tunda akwai kiyayya a tsakani they will use every means possible to get it" taji ajjiyar zuciya"to yanzu ya zan yi? How can I get rid of them? Ko gida zamu chanja ne?" Yace "yadda suka gano wanna gidan idan mun chanja ma haka zasu gano shi. But we will take security measures for protection" Sun jima suna magana akai sai ya fita, ta koma ta kwanta, sai ta tuno da maganar Hajiya Maryama years back, ta sake tashi ta zauna, yanzu idan ta mutu bata haihu ba duk abinda ta tara a duniya su yaya Malam ne zasu gada? Except for 1/8 da za"a cirar wa Adam. Three weeks after that maganar tafiyar su Beijing ta tabbata. Wani taron karawa juna sani ne na wani international organization na yan kasuwa, anan ne aka bawa Safiya dama tayi magana da yawn small scale entrepreneurs na Nigeria da kuma irin kalubalen da suke fuskanta. A cikin bayanan nata ne ta bada labarin ta da yadda ta rasa iyayen ta da yanuwanta da kuma yadda ta fara kasuwancin ta hanyar suyar awara a kofar gidan su har zuwa matakin da take kai a yanzu, Bayanan nata sun taba zuciyoyin mutane da yawa a fadin duniya baki daya, aka bata award suka yi pictures da mutane da dama, mutanen da ada take gain sunyi mata nisan da ko hanya ba zasu hada da ita ba. And kamar yadda Adam ya gaya mata, she got a lot of contracts and connections, a ciki wanda tafi jin dadin sa shine na wani textile industry da suka yi mata alkawarin zasu zo su bude branch a Nigeria and she will be their lead. Ita zasu bawa contract din tun daga selection na site din da zasu yi ginin industry din har aikin ginin, siyo machineries da kuma daukan ma'aikata. Bata dauka da gaske suke ba sai da suka dawo Nigeria taga sun kira sun cigaba da maganar. Nan da nan ta hau hidima tare da taimakon Adam. She got an opportunity and she used it wisely. Ta tsaya tayi musu aiki akan gaskiya da gaskiya and she got their trust har suka sakar mata kudi sosai. Ta kuma yi amfani da damar wajan kyautatawa du wadanda suka yi playing major roles a rayuwar ta, kusan aikin tun daga farkon sa har karshen sa da Alhaji Nasir da Hajiya Maryama aka yi shi. Cikin shekara daya aiki ya kammala, a gurin kananan ma'aikata ta bawa mutanen ta dama sosai, a lokacin ta samu fada sosai a gurin yan'uwan Adam dan ta dauke su sosai har sai da Adam yayi mata magana yace sunyi yawa, ta aika wa da Hajiya Kyauta slots ita ma tace in tana da wadanda take so a bawa aiki ta turo su ayi musu interview, Hajiya Kyauta kuwa ta turo yayanta da jikokin ta sosai kuma kowannen su aka bashi inda ake ganin ya dace da qualifications dinsa da kuma experience din sa. She then send slots to makotansu, wadanda suka taimakawa Baba Hadiza a lokuta da dama sanda tana raye, bayan rasuwar ta ma kuma they were kind to them, suma suka aiko samari biyu a gidan kuma Safiya ta basu aiki suma. A lokacin ne ta sake yin baki. Ranar tayi baccin safe ba ta tashi da wuri ba, Adam kuma yana Kano suna shirye shiryen bikin kaninsa Ahmad da aka kusa yi. Ta tashi ta shirya tsaf da niyyar zuwa gidan Hajiya gurin Sa'adatu, tana saukowa daga stairs idanunta suka sauka akan yaya Malam da Dauda a zaune a kan kujerun ta na falo, Ta tsaya tana kallon su, suma kuma motsinta ya saka suka juyo suna kallon ta, sai suka mike a tare suna washe mata baki, Dauda yace "ga antin namu nan ta sauko, An sha bacci" yaya Malam yace "ba dole tayi bacci ba, wanna hidima haka". A dai-dai lokacin da daya daga cikin ma'aikatan gidan ta shigo ta ajiye musu drinks da fruit a cikin plate. Tana mikewa Safiya ta kira sunan ta "Hassana, waye ya shigo da wadannan cikin gidan nan? Dawo kizo ki duke min lemo na ki mayar da shi fridge ko kuma ki bawa almajirai a waje" yadda tayi maganar cikin fada yasa yarinyar ta rikice, dan basu saba jin Hajiyar ta su ta daga murya ba. Ta dawo hannu yana rawa zata dauka Dauda ya mike "ke! Zan kwarfe ki anan gurin in kika taba wallahi" ta ja da baya a tsorace tana kallon Safiya. Safiya ta nuna mata hanyar waje "kira min mai gadi" har yarinyar tayi hanyar waje sai kuma tace "barshi ma, zo kiyi tafiyarki", ta tuna cewa ba wancan mai gadin bane ba, su biyu ne masu gadin nasu kuma shifting suke yi, so wanna bai san yaya Malam ba, and the girl was greatful to go. Ta tsaya at the foot of the stairs ta rungume hannayen ta a kirjinta tana kallon yadda suke rige rigen cin abinda aka ajiye a gabansu, "Safiyan Baba Hadiza kenan, Safiyan Baba, kai Allah dai yaki kan Baba, Baba zai ji dadi idan da ace zai ganki a yanzu, kinyi kyau abinki, Baba zai ji dadi idan da ace zai gan mu a yanzu tare da ke, yayye sun kawo wa karamar kanwarsu ziyara. Kai zumunci yayi", Ta saka hannu a jakarta ta dauko wayarta ta nemo number din dpo din police station da take kusa da su. Wancan zuwan da su yaya Malam sukayi a cikin matakan da suka dauka ita da Adam akwai reporting issues din to the police station nearest to them cewa akwai wadanda sue bibiyarta kuma suna tsoron kar su cutar da ita, sai dpo din ya rubuta case din kuma ya basu number din sa akan cewa in suka sake zuwa ta kira shi direct. Ta danna kira ta saka a kunnen ta still idonta yana kan su Dauda, yana dauka tace "hello dpo" suka gaisa ta fara yi masa bayanin ta yace ya gane ta ai. Sai tace "the people I once lodge a complain about are here again, they are threatening my life and frightening my house staff. Okay. Thank you. Ina jiran ku" and she hing up and continued standing up and staring at su yaya Malam. Dauda yana kallon ta shima ya taba yaya Malam yace "yaya me take cewa ne, kai ka dan fini iya turancin" yaya Malam shima yana kallon ta fuskarsa cike da takaici da mamaki yace "yan sanda ta kira mana, tace su zo su kama mu wai munzo zamu kashe ta" Dauda ace "kut...... To ke idan kashe kin zamu yi ai da tuni kina lahira wallahi. Shikenan ba zamu zo gidan ki muyi zumunci da je ba sai ki ce zamu kashe ki? Da tun kina jaririyar ku bamu kashe ki ba sai yanzu?" Still bata ce komai ba sai ma gyara tsayuwar ta da tayi ta cigaba da kallon sa, yaya Malam yace "ko magana fa bamu isa tavi mana ba. Bamu isa tayi magana da mu ba. Lallai kudi masu gidan rana. Ko ba zakiyi magana ba na san ai kina jina tunda ke ba kurma ba ce ba, mu yan uwanki ne uba daya ya haife mu kuma munzo neman taimako gurin ki. Safiya ko abincin da zamu ci bamu da shi amma ke kina nan kina rabawa mutanen gari wanda babu dangin ¡ya babu na baba manyan aiyuka, kina zaune a wanna katon gidan, kalli irin abincin da kike ci...' " Ya fada yana nuna [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Dauda yana kallon ta shima ya taba yaya Malam yace "yaya me take cewa ne, kai ka dan fini iya turancin" yaya Malam shima yana kallon ta fuskarsa cike da takaici da mamaki yace "yan sanda ta kira mana, tace su zo su kama mu wai munzo zamu kashe ta" Dauda ace "kut...... To ke idan kashe kin zamu yi ai da tuni kina lahira wallahi. Shikenan ba zamu zo gidan ki muyi zumunci da je ba sai ki ce zamu kashe ki? Da tun kina jaririyar ku bamu kashe ki ba sai yanzu?" Still bata ce komai ba sai ma gyara tsayuwar ta da tayi ta cigaba da kallon sa, yaya Malam yace "ko magana fa bamu isa tavi mana ba. Bamu isa tayi magana da mu ba. Lallai kudi masu gidan rana. Ko ba zakiyi magana ba na san ai kina jina tunda ke ba kurma ba ce ba, mu yan uwanki ne uba daya ya haife mu kuma munzo neman taimako gurin ki. Safiya ko abincin da zamu ci bamu da shi amma ke kina nan kina rabawa mutanen gari wanda babu dangin ¡ya babu na baba manyan aiyuka, kina zaune a wanna katon gidan, kalli irin abincin da kike ci...' " Ya fada yana nuna abinda aka kawo musu, "amma mu hatsin da zamu dama wa yaran mu kunu su sha safiya gagararmu yake yi. Inna Gaje ta rasu. Inna Sa'ade tana bukatar taimako kuma kina da halin da zaki taimaka mata, zaki iya kaita asibiti ayi mata kafar katako ko ki siya mata keken guragu ko kuma ki daukar mata mai kula da ita, duk zaki iya. Mu kuma ki sama mana aikin yi Safiya. Ga yayanki nan Dauda ko gidan da zai ajive iyalinsa ba shi da shi a yanzu sai gida matar ta shi ta koma. Ki daure ki bashi ko da aikin gadi ne. Ga su Haruna nan da badamasi duk basu da wan takamaiman aiki. Ga danki nan Salisu shima ya gagara yin aure saboda rashin aikin yi. Ki taimaka mana kamar yadda Allah ya taimake ki ya mayar da ke yadda kike din nan". Ko motsa bakinta bata yi ba ballantana tace masa kala. Ya mike tsaye zuciya tana cinsa yace "lallai yau kin tabbatar min da abinda nake zargi a kanku, cewa ku shegu ne ba yayan baban mu ba. 12 9 4 10:03 PM Dan babu dan uwan da zai viwa dan uwansa irin wannan wulakancin, jini ai ba wasa bane ba" Dauda shima ya mike ya doso ta "tunda tace kashe ta muka zo yi gwara in kashe ta din ai shikenan kowa ya huta" yaya Malam ya rike shi "kar ka taba ta. Tarko ta dana mana so take mu taba su taji dadin rufe mu. Kar ka jefa mu a tarkon ta, Wanna yarinyar shaidaniya Ce" Dauda ya kwace daga hannu sa ya karasa gabanta suka tsaya suna kallon juna, ko motsawa bata yi ba, sai kuma yayi murmushi yace "an gaya mana ai, an fada mana cewa ke juya ce ba kya haihuwa. Ki cigaba da tara mana dukiya kinji? Kina mutuwa zamu zo mu kwashe tas. Allah ne ya bamu", Ya juya ya saka kafa yayi ball da drinks din da aka ajiye musu sannan ya fita yaya Malam yana bin sa a baya. Sai da suka fita sannan ta saki numfashin da ta rike tun sanda Dauda ya kira ta da juya, a take jikinta ya dauki kyarma har saida ta kasa cigaba da tsaiwa ta zauna a kasa tana ruke da kirjinta, zuciyar ta zafi take yi mata. A haka police din da ta kira suka karaso suka same ta, ba ta iya tayi musu bayanin komai ba sai yarinyar ta Hassana ce ta zo tana kwatanta musu kamannin wadanda suka zo din da kuma kayan jikin su, aka kira mai gadi shima yayi bayani sai kuma ya kara da cewa "sun gaya min su yanuwanta ne daga garinsu suke shi yasa na barsu suka shigo, kuma naga suna kama, kama irin ta jini". A ranar Adam yana jin labarin abinda ya faru ya juyo daga Kano, yana zuws ya zarce dakinta da sauri yaje ya rungume ta, sai da taji dumin jikinsa sannan ta saka kuka. Ya bar ta tayi kukan ta ta gama sannan tace "sunce ni juya ce ba na haihuwa, sun ce ina mutuwa zasu zo su kwashe duk abinda na tara. And they will do that idan na mutum" ya girgiza ta "and who told you zaki riga su mutuwa? Waye ya san gawar fari? Kuma waye ya gaya miki ba kya haihuwa?" Ta bude hannun ta "to ina yayan suke? Gaya min suna ina? Nuna min su" ya girgiza kai "'it has been just four years. Babu wanda zai ce bama haihuwa dan muni shekara hudu bamu haihu ba. And if it will put your mind at rest zamu iya zuwa orphanage muyi adopting baby, baby sabuwar haihuwa yadda babu wanda zai ce bamu muka haife shi ba. Wannan zai dakatar da su daga irin wadannan threats din". Ta sake girgiza kai. "We can fool them. Amma Allah yasan ba namu bane ba kuma ba shi da gadon mu" yace "Okay then. We can start fertility treatment in kina so, duk da dai ni nasan lokaci ne bai vi ba. Ga Sufyan nan da matarsa Hajjo sun riga mu aure amma basu haihu ba suma har yanzu. Akwai couples da na sani da suka yi shekaru ashirin basu haihu ba daga baya kuma suka haihu. We should just be patient Safiya, muyi ta gayawa Allah zai dube mu ya share mana hawayen mu". Wannan maganar ta kara kusanci mai karfi tsakanin Hajjo da Safiya, they understood each other irin tunda suna cikin the same situation, a hankali har suka koma kawance, daga baya kuma suka koma aminci yadda kowa ta san komai na kowa. They support each other through ups and downs. Exactly a year later matar Ahmad kanin Adam ta haihu, wata goma bayan bikin su, ta haifi dan ta namiji aka saka masa suna Mukhtar. A shekarar ne kuma finally Sa'adatu ta gama ruwan idonta ta zabi miji, kamar yadda ta jima tana mafarki, babban mutum ta zaba, wani dan majalisa acan garin su Katsina amma anan Abuja ya sama mata gida zata zauna a matsayin ta na amarya, matar sa kuma ta farko tana Katsina. Aka yi bikinta, Safiya tayi mata zumunci sosai ta tare a gidan mijinta. Daga nan suka cigaba da zumuncin su. A shekarar ne kuma ta sake yin baki daga Kura. Wannan karon ba maza bane ba mata ne. Lami da Lantana. Ranar ta dawo daga unguwa mai gadi ya gaya mata tayi baki mata, bata yi tunanin komai ba saboda akwai wadanda take expecting kuma dama ta gaya wa security din gidan cewa wasu mata zasu zo neman ta, wani program ne take leading a lokacin na wani ngo da zasuyi training mata a bangaren catering, 19 3 10:03 PM Sai dai tana shiga sai ta tarar ba matan da take tunani bane ba. Lami ne da Lantana da kuma mata duburwar yarinya da take Safiya ta gane ta saboda ta sha wahala a gurin rainon ta sanda tana baby. Ta tsaya kawai tana kallon su a zazzaune akan kujerun ta. Lantana tana yiwa yarinyar magana a hankali can kasa yadda ba dan falon yayi shiru ba da Safiya ba zata iya ji ba "kin dai gane duk abinda muka gaya miki ko? Mu mun san abinda zamu ce mata yanzu ta karbe ki, in dai har muka samu ta yarda kika zauna a gidan shikenan mun samu abinda muke bukata" Sai kuma Lami tace "wai ni a ina kike ganin yarinyar nan ta samu wannan uban kudin ne?" Lantana tace "kin manta an tabbatar mana da cewa Hajiya Kyauta ce ta fitar da ita daga gari? Kin manta kuma safarar yammata dama take yi? Ai kasar waje take kai su suyi karuwanci su samu kudi, an ce fa a wajen har karnuka ake hada su da su sai kuma a basu miliyoyin kudi" Cikin bacin rai Safiya ta kwala kiran mai gadi, ranar duk masu gadi biyun ne a gidan, suka taho a guje cikin tashin hankali, ta nuna su Lami "waye ya shigo min da wadannan mutanen cikin gida na?" Daya yace "Hajiya bakin ki ne da kika ce zasu zo, su suka ce mana su bakin ki ne" tace "wadannan fa sune bakin da na ce kar a sake bari su zo min gida, wadanda nace in sun dawo a harbe su" mai gadin ya bude baki cikin mamaki "Hajiya wallahi bamu gane su ba. Gidan nan mutane suna shiga suna fita kullum, ba zamu iya gane kowa ba" ta dauko wayarta daga cikin jaka ta juya gurin su Lantana tace "ku dan kalle ni kadan" suka juya suna kallon ta sai ta dauke su a hoto, ta juya gurin masu gadin tace "ga hoton su nan zan tura muku, kuyi ta kallon hoton har ku gane kamannin su, ko su ko masu kama da su bana son gani a jikin gidan nan ballantana cikin gidan nan. Idan kuma kuskure irin haka ya sake faruwa zaku rasa aikin ku" Ta juya da sauri ta doshi stairs Lami ta mike da sauri ta rike hannunta "haba kanwata, wai me muka yi miki haka mai zafi ne. Ubangiji yana son zumunci kuma yana son masu sada shi, sannan kuma baya son masu yanke shi. Mu kadai kike dasu kaf duniya. Bana son yadda kike zaune a garin nan baki da kowa naki a tare da ke. Shi yasa muka kawo miki yarki ta zauna a gurin ki dan mu gyara zumuncin da yake tsakanin mu. Allah yaji kan mahaifin mu", Wani mugun kallon da Safiya take binta da shi ya saka ita da kanta ta saki hannun ta fara ja da baya tana girgiza kanta. Lami tace "duk kiyayyar da kike yi mana ba zaki taba cire jinin mu da ga jikin ki ba, ba zaki taba cewa mu ba vanuwanki bane ba" Safiya ta juya tana kallon security dinta "'ku je ku kunto karnukan nan daga cikin kejin su ku hada su dasu su fitar da su in ku ba zaku yi ba" ta kalle su tace "maybe in suka hadu da karnukan zasu fahimci wahalar da ake sha kafin ayi kudi" a take suka fara rige rigen fita daga falon har suna yin tuntube da juna. Sai dai har sun kai bakin kofa Lami ta juyo tana kallon ta tace "lokacin da zamu dawo yana nan zuwa, ko bama raye zamu bar wa yayan mu wasiyyar su zo su karbi gadon ki in kika mutu. Kuma dole zaki mutu, dole kowa zai mutu". Shekaru biyu bayan auren Sa'adatu ta haihu ta haifi namiji aka saka masa Mustapha, a lokacin kuma matar Ahmad ita ma ta kuma haihuwar namiji aka saka masa sunan Adam. Sanda suka je barka ita da Adam sai Ahmad ya kawo masa dan "yaya nayi maka takwara, idan an yaye shi ni da mamansa muni alkawarin bar muku shi tunda babu yara a gurin ku" yayi shiru yana kallon su sai kuma ya kara da "kafin ku samu naku" suka sake yin shiru sai ya sake cewa "in kuma Mukhtar kuke so sai mu baku shi tun yanzu, tunda yayi wayo already" Safiya tayi ajjiyar zuciya tace "mun gode sosai Ahmad, Yaran ai duk namu. Allah ya raya du yayi musu albarka" Shekara daya bayan nan Allah ya albarkaci Sufyan da haihuwa shima ya samu namiji, aka saka masa Abdul Hakim. Haihuwar Abdul ta dan daga hope din su Safiyya, sai kuma a lokacin ta yarda suka fara fertility treatment. 15 8 10:03 PM Ita duk tsahon lokacin nan tashin hankalin ta shine kar taje asibiti ayi mata confirming cewa ba zata taba haihuwa ba, without knowing she was holding on to hope cewa zata haihu watarana. Shekaru suka cigaba da tafiya, har Safiya da Adam suka shekara goma da aure, babu ciki babu labarin sa, sai war dukiya da take ta ninka kanta both a side din adam dana Safiyya. Ita kanta kudin da take dashi toro yake bata in ta zauna tana lissafin sa, a anniversary dinsu na shekara goma da aure ne suka bude their first personally owned textile factory, two years after that suka bude na takalma da jakankuna and that was in addition to all the other companies da suke da manyan hannayen jari a ciki, one of the major one of which is the gold company wanda har yau Safiya ba ta taba taba share dinta ta ciki ba, it just kept growing, Safiya tayi charity da yawa a tsahon rayuwar ta, most of which tana yi ne da sunan mahaifiyarta, wasu kuma tana yi da niyyar neman haihuwa. And deeply in her tana jin wani assurance na cewa adduoin ta ba zasu tafi a banza ba, that she will one day get a child. Five years haihuwar Mustapha Sa'adatu ta sake haihuwa ta haifi mace ta saka mata Safina. Safiya ce ta kaita asibitin haihuwar kuma a hannunta aka haifi Safina. Sa'adatu tana labour tana yiwa Safiya addu'ar samun haihuwa har Safiya tana tsokanar ta cewa bata in ciwon haihuwar shi yasa. Ranar suna aka saka wa yarinyar Safina, Sa'adatu tace wa Safiya "sunan ki fa na saka a wayan ce, bana son saka mata Safiya Hajiya ta saka ni a gaba tace dan kudin ki na saka mata sunan ki, kin san Hajiya gani take kamar nafi kowa son kudi a duniya" Safiya tayi dariya tana kara rungume yarinyar "Safina is my daughter, ko taci suna na ko bata ci ba". Sam yan'uwan Safiya basu barta ba, an sha gaya mata cewa an ga Dauda ko wani daga cikin su around unguwar su, sai da suka kai pictures dinsu duk gurin yan sandan da suke kusa da su sannan suka kara security din gidan. Gidan ya koma duk wamda zai shiga sai any waya cikin Sam yan'uwan Safiya basu barta ba, an sha gaya mata cewa an ga Dauda ko wani daga cikin su around unguwar su, sai da suka kai pictures dinsu duk gurin yan sandan da suke kusa da su sannan suka kara security din gidan. Gidan ya koma duk wamda zai shiga sai any waya cikin And then two years later all of a sudden Safiya became pregnant. Ranar da taje asibiti suka yi confirming pregnancy dinta wuni tayi tana kukan jin dadi, da daddare kuma kasa rufe idonta tayi dan gani take kamar tana rufe idon zata farka ta ga cewa ashe mafarki take, sai ta raya daren wajan godiya ga Allah a bisa wannan kyautar bazata da yayi mata. Mutane sun kasa gane tsakanin Adam da Safiya waye yafi murna da cikin nan, waye kuma yafi son cikin, su kan su basu sani ba. In celebration of samun cikinta ta shirya bikin bude sabon gidan gonar ta data sanya wa suna "The Oasis",. Gidan gona ne da yake da bangarori daban daban, akwai bangaren kiwon kaji layers akwai na broilers, akwai gurin kiwon raguna akwai kuma na kifi, sannan ga side din exotic animals wadanda aka saka su dan su kawara gurin kuma su zama ababen debe kewa. Sai kuma aka yi shuke shuke shuke na different varieties of fruits. Aka dauki masu aikin gidan gonar aka yi musu dakunan su a gefe. Kusan a cikin The Oasis akayi renon cikin Safiya, dan tunda aka bude gidan gonar Safiya ta dauki son duniya ta dora masa kullum acan take wuni. Sometimes har kwana suke yi a dakunan da suka ware saboda hakan. A haka har cikin ya girma kuma ya isa haihuwa, da kyar Adam ya raba ta da Nigeria ya kaita america ta haihu a can saboda yana son babyn ya samu citizenship na can. "For the rainy days" ya fada a kokarin sa na convincing dinta. Sai dai ita a lokacin concern dinta shine gender din abinda zata haifa. Adam yace "kina nufin saboda ba kya son yan'uwanki su gaje ki ba kya son ki haifi mace?" Ta girgiza kai "ko me a haifa zan so shi fiye da raina. q 10:03 PM Amma idan suka ji na haifi namiji zasu fita daga rayuwa ta, shine kawai abinda nake bukata" sai kuma ta kara da "'kuma in na mutu ba zasu ci kwandala ta ba". Adam yaji ransa ya baci "wai ke baki da magana sai ta mutuwa? Why do you always want to torment me with maganar zaki mutu?" Tayi murmushi "duk zamu mutu. Kowa zai mutu" Ranar da Safiya ta haihu was the happiest day of her life. Ba ta taba dauka cewa a duniya akwai farin ciki irin wannan ba. A lokacin shekarun su goma sha biyar da aure. Ita kuma shekarar ta arba'in a duniya. Ta rungume jaririyar tana kallon ta hawayen farin ciki yana fita daga idonta, tana kallon Adam yana yi musu pictures, ta shafa fuskar yarinyar tace "she looks just like Baba Hadiza, dan Allah Adam ka saka mata Hadiza" ta dawo kusa da ita yana kallon jaririyar yace "she looks just like you, na baki wuka da nama, ki zaba mata duk sunan da kike so" ta fara murna kamar zata vi rawa "Hadiza zan saka mata, Baba Hadiza zata ji dadi sosai idan taji nayi mata takwara" ta sake dariya "na san Khadijah ma cewa zata yi sunan ta ne" sai kuma ta bata fuska tana tunani "Sauda ba zata ji dadi ba, ita rigimammiya ce ga saurin kuka, zata ce ita ban saka sunan ta ba" Adam yayi dariya "kina da abin dariya wallahi, Yanzu a lahirar ne har za'a yi rigima da kuka?" Sai da ga mamakin sa har cikin dare da ya farka yaga Safiya tana zaune tana feeding baby ya zo ya zauna a kusa da ita sai cewa tayi "sunan Sauda kawai zan saka mata, maybe idan nayi haka zata yafe min fitar da nayi na barta a daki ita kadai" Da safe kuma "na fasa saka Sauda Hadiza za'a saka, sai a ringa ce mata Kubra, ka ga ai ba sunan kowa bane ba" ya saka hannu ya dauki jaririyar daga cikin gadon ta ya zauna akan kujera yayi mata huduba sannan ya mayar da ita ya kwantar yace "nayi mata huduba da sunan ki. Because I love you so much, kinga yanzu babu zancen explanation". Shikenan yarinya taci sunan mamanta, sai dai aka chanja sunan ya koma Safiyya instead of Safiyya, a hankali kuma sai aka sake mayar mata da shi Fiyya. Sai da Fiyya tayi sati biyu a duniya sannan suka dawo Nigeria bayan uwa da yar sun huta sosai. A lokacin Safiya ta fahimci irin yawan mutanen da take dashi da irin soyayyar da mutane suke yi mata, dan har sai da ta rasa inda zata saka kayan baby, mutane kuwa kullum gidan a cike yake da yan zuwa barka tare da fatan alkhairi. Hajjo da Sufyan ma sunzo daga Berlin inda suke zaune tare da little abdulhakim sunga baby. Sa'adatu kuwa kamar ita ta haihu dan tattaro yayanta tayi suka dawo gidan Safiya sai tazo zaman jego. Babu wanda ya isa ya taba yarinyar nan, ganin ta ma sai dai mutum ya leka a hannun ta ya gani amma ba zata bayar ba sai dai in anfi karfin ta. Sam Safiya bata jin kewar wai bata da yan'uwa a duniya, ita mantawa ma take yi cewa bata da yan'uwa. Sai dai wata daya da haihuwar tata aka aiko mata da sako a cikin envelope. Ta dauka masu aiko da barka ne wadanda suke jin nauyin bayarwa hannu da hannu. Ta karba ta bude sai taga takarda ce da rubutu marar yawa a ciki, ta karanta "Muna taya ki murna. Ashe munyi ya, Allah ya raya ta. Muna nan muna jira, ko bamu samu ba yayan mu zasu cigaba da bibiya har zuwa ranar da zasu samu. Kowa zai mutu, sai dai ba kowa ne zai haifi namiji kafin ya mutu ba". Ta ajiye takardar tare da kafa wa jaririyar hannunta ido. Ta gane daga ina takardar ta fito ta kuma gane abinda sakon yake nufi. And in one minute ta yanke hukunci. A daidai lokacin Adam ya shigo dakin, Yana kallon fuskarta ya san something is wrong, Ya karaso da sauri yana duba lafiyar Fiyya sannan ne ya lura da takardar da take gabanta ya dauka ya karanta, Yayi zagi kasa kasa tare da juyawa da sauri zai bi baasin wanda ya kawo takardar sai sai ta dakatar da shi "don't bother. Kwandala ta ba zasu ci ba. Ina son magana da kai" ya dawo ya zauna yana kallon ta sai tace "na yanke shawara, ina fatan kuma zaka goya min baya" ya gyara zama "wacce shawarar ce?" Tayi murmushi tana shafa fuskar Fiyya "all what I did a rayuwata, tun bayan mutuwar Sauda, duk wani decision da na dauka a rayuwata all the struggles all the wealth and all the tears were 25 11 4 10:03 PM for her. Duk dan Fiyya nayi komai. She is my dream and my legacy. She is everything I have ever hoped for. She is my future, and the future of my family" cikin rashin fahimta yace "still ban gane me kike nufi ba. Menene shawarar da kika yanke?" Ta dago kai tana kallon sa tace "I am going to transfer everything I have, I mean everything down to the last kobo, to her name". Ya bude ido yana girgiza kai "that is not possible" tace "it is. Babu abinda yake not possible a rayuwa, Ita kadai ce ya ta kuma daga kanta ba zan kuma haihuwa ba. All what I need to do is to get my lawyers to change everything daga Safiya Khalid to Safiyya Adam Muhammad, shikenan" Ya rike hannun ta "is it about maganar gadon nan wai? Shin wai ba sai mutum ya mutu ba sannan za'a ci gadon sa? Are You sick? Akwai abinda yake yi miki ciwo ne?" Ta girgiza kai "babu abinda yake damuna. In fact I have never felt as amazing as I am feeling right now. Na riga na yanke shawara all I need is your trust and support" yace "amma Safiya I am afraid for Fiyya, what if suka ji abinda kika yi and they harm her and then you? Babu abinda mutanen can ba zasu iya yi akan dukiyar nan ba, babu abinda mutane da zasu iya yi akan dukiya ba". Ya sunkuyar da kanta tana kallon Fiyya da ta bude ido ita ma take kallon ta, she then smiled and say "no body will harm her saboda yaci dukiyar ta. Nobody will harm my daughter" ta fada tana shafa gefen fuskar Fiyya sai kuma ta dago kai tace "I will sign another contract with my lawyers" Adam yace "na menene kuma?" Tace "if anything is to happen to Safiyya Adam Muhammad wanda zata rasa rayuwar ta, be it natural death ko suspicious death kafin ta samu magadan ta, everything in her name will go to charity". Adam ya bude baki da hanci yana kallon Safiya da mamaki, but she had that stubborn look da yasan cewa ta riga ta gama magana. Ta cigaba da cewa "ina so ka tabbatar kowa da yake kusa da ita ya san da wannan maganar, that way, people will take care of her and make sure babu abinda ya same ta, ko ba dan Allah ba ko dan dukiyar ta". Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA❤️‍🩹 Episode Thirty Three : The Oasis (U 6 Paid Advert Yar uwa kinsan illar dake tareda infection kuwa,to bari kiji kadan daga cikin illar da infection yake da ita, kinsan cewa infection yana hana haihuwa,yana hana ma'aurata jindadin mu amala,yanasa warin gaba kowane irin tirare kika sa bazai hana wannan warin fita daga jikin kiba fitar farun ruwa kaikayin gaba tusar gaba duk suna daga cikin illar da infection yakewa Ifyr ki. Ina masu fama da ulcer, Asthma,sickle, ina matar dake fama da fibriod, matsalar rashin haihuwa ko bushewar jiki da fata haddake mai son hibs da breas ina uwar gida maison faranta ran oga a othe room kema ba abarkiba jawarawa da yanmata ku garzayo kuma ku kwada ku gani munada feminine wash,garlic oil da dai sauransu munada VIP chair akwai blood circulatory machine ga kuma data1g250 cikin sauki da rankwame da rahusa kedai kira number nan domin karin bayani 07035275119, 08038098317 Adam yayi shiru yana kallon ta yana kuma nazarin maganganun ta, a karshe sai yace "you can gift dukiyar ki to her, but you cannot give a will na cewa idan ta mutu kafin ta samu yaya a kai dukiya charity, it is not islamically possible. In dai kin bata then you no longer have the right to dictate yadda zata yi da ita. Zata iya duk abinda ta ga dama da ita. And ko da ita din ma, bata da damar cewa ga abinda za"a yi da dukiyar in ta mutu, tana dai da damar tayi abinda taga damar yi da ita idan tana da rai, kamar yadda ke ma yanzu zaki yi abinda kika ga damar yi da ita yanzu da kike da rai". Tayi shiru tana tunani, ta san cewa gaskiya ya fada, ta dago kai tana kallon sa, she still had that stubborn look a tare da ita "bana son ta zama target na mutane saboda dukiyar ta, bama so mutane su cutar da ita saboda dukiyar ta. In haka ta faru na zalunce ta" ta danyi shiru sai kuma tace "I will still sign the contract" yace "how? Zaki ketare iyakar ubangiji kenan?" Tayi murmushi "no. I will forge the contract. Zamu gayawa mutane cewa munyi agreement da lawyers din da suke kula da dukiyar cewa zasu bayar da ita ga charity idan Safiyya ta rasa ranta kafin ta haihu. We will make them think and believe that. While in reality ba zamuyi hakan ba. We will make them take care of her ko dan su amfana da dukiyar ta, knowing idan wani abu ya same ta zasu rasa both ita and the money", Adam yace "I don't know why you are saying "they', Mu zamu kula da yar mu and we will raise her together. Su kuma wadanda kika yi haka saboda will never get close to har ballantana har su kula da ita. Ban fahimci suwa kike nufi ba" tace "every body. In nace 'they' ina nufin everyone. Akan issue din Fiyya da dukiyar nan ban yarda da kowa ba sai kai sai Hajiya. Ko Sa'adatu ban yarda da ita ba, ban yarda da yan'uwan ka ba, ban yarda da duk wanda zai zo kusa da ita ba. Ba wai cewa nayi su ba mutanen kirki ba ne ba, but money can change people or sometimes it brings out their true color. It can corrupt even the most purest of hearts sai wanda Allah ya kare. Yana daga cikin challenges da masu kudi suke fuskanta cewa basa iya gane wanda yake son su saboda Allah da kuma wanda yake son kudin su. Kana ganin da bani da kudin nan yan'uwanka zasu yi shiru a lokacin da nayi shekaru goma sha biyar a gidan ka ba tare da na haihu ba? Har kuma su dauki babyn da suka haifa suce sun bani kyauta?" ya yi kokarin defending dan uwansa "Ahmad have been managing businesses din mu for ears, bamu taba samun matsala ba" tace "saboda akwai masu monitoring shige da fice da kudi. Ka fahimce ni, ba nace ina zargin Ahmad ba ko kuma nace shi ba mutumin kirki ba ne ba, am just saying kudi most of the times shaidan ne. It can corrupt him. Musamman yanzu idan za'a yi wannan transfer of ownership din dole zai sani saboda yana managing bangarori da yawa na dukiyar. 20 14 9:19 PM Ahmad bashi da gado na but in na bawa Fiyya na matso da kudin toward him, I want him to believe idan wani abu ya same ta nobody is getting anything, I want everyone that will ever come close to her to believe that, ko nan gaba zaka yi aure zaka haifi wasu yayan I want the wife and the children to believe that, ko ta girma zata yi aure I want the husband to believe that". Adam ya dafe kansa yana jin yana sara masa, shi kansa duk ciwo yake yi masa with all these lissafi marar tishe da take yi. She is alive and well, babu amfanin wadannan lissafe lissafen, Yace "Okay, please stop talking as if kina bankwana da duniya ne, kina saka wa ina kasa gane komai. You have been talking and now it is time for me to respond. Macanar for you to have a peace of mind cewa mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba. And maganar charity bla bla bla, shima zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar gaskiya zaki yi signing ba. But magana daya zan kara akai, Koma me kika yi I do not want Fiyya to know. I want her to have a normal childhood and grow up to be stronger than even you. I don't want her to grow up with this burden on her shoulders. Har sai ta girma ta mallakin hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda zata kula da kyautar da kika yi mata sannan zata sani. If you agree to this than everything else is fine with me". And that was how the agreement was concluded and within months aka gama komai. Everything da Safiyya ta mallaka wanda yake da takardar shaidar mallaka sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya Adam Muhammad. Tun daga kan shares dinta in factories din su ita da Adam har kan wadanda take da outsiders, har aka sauko kan personal belongings dinta su sarkokin ta da motocin ta and every other valuable possession, Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a lokacin ya sani, kamar yadda kuma a gabansa tayi signing takardar bogin da ta komai. You have been talking and now it is time for me to respond. Maganar transfer of ownership na yarda kiyi, just for you to have a peace of mind cewa mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba. And maganar charity bla bla bla, shima zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar gaskiya zaki yi signing ba. But magana daya zan kara akai. Koma me kika vi I do not want Fiyya to know. I want her to have a normal childhood and grow up to be stronger than even you. I don't want her to grow up with this burden on her shoulders. Har sai ta girma ta mallakin hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda zata kula da kyautar da kika yi mata sannan zata sani. If you agree to this than everything else is fine with me" And that was how the agreement was concluded and within months aka gama komai. Everything da Safiyya ta mallaka wanda yake da takardar shaidar mallaka sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya Adam Muhammad. Tun daga kan shares dinta in factories din su ita da Adam har kan wadanda take da outsiders, har aka sauko kan personal belongings dinta su sarkokin ta da motocin ta and every other valuable possession, Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a lokacin ya sani, kamar yadda kuma a gabansa tayi signing takardar bogin da ta rubuta da kanta cewa if anything is to happen to Safiyya Adam Muhammad komai in her name will go to charity. And after doing all that, Safiya became happier and more relaxed. Ta mayar da hankalinta kachokam kan kula da jaririyar yar ta wadda tafi so fiye da rayuwar ta. A cikin watannin ne kuma kaddara ta saukar wa Sa'adatu. Mijinta uban yayan ta yayi accident ya mutu. Wannan mutuwa ba karamin daga hankalin Sa'adatu da duk wanda yake tare da ita tayi ba. Ya tafi ya barta da 8 years old Mustapha and 2 years old Safina. And Safiya was there for her, a kan kafadun ta Sa'adatu tayi kukan rashin mijinta, a gidan ta kuma tayi spending most of her moaning period. Sai dai kuma tun kafin ta fita daga takaba efcc suka dira a gidan ta suka kore su daga ciki suka garkame gidan da sunan yana under investigation. Sannan kuma suka yi freezing account din mijin. Shawarar da Safiya ta fara bata sanda tazo gidan ta tana kuka tana gaya mata abinda ya far shine ta koma gidan Hajiya ita da yaran for the mean time kafin a warware problem din amma Sa'adatu ta girgiza kanta "ba zan iya komawa gidan Hajiya ba, ga yara" Safiya tace "me zai hana? Hajiya tana rike wadanda bata da hadi da su ma ballantana su Mustapha da suke kamar jikoki a wajenta" Sa'adatu ta sake girgiza kai "duk wanda ya riga ya wuce age din zama a gida ya riga ya wuce. Ina komawa raini ne zai shiga tsakani na da mutanen da suke gidan" Safiya tace "to ki zauna anan, akwai isassun dakunan da ba zaku takura ba daga ke har yara" shima Sa'adatu ta ki yarda tace "ba zan zo in zauna miki a gida ba ga mijinki yana gidan". A karshe sai ta tattara kudin duk da take da shi a account dinta ta kama rent din gida a nan Abuja duk kuwa da yadda Safiya ta nuna kin amincewar ta da maganar. "In kika karar da kudin hannunki akan rent da me kuma zaki biya wa yara kudin makaranta da me kuma zaki cigaba da rayuwa? Wannan kudin da hannun ki kamata yayi ki juya shi, this is the right time to fold up your sleeves and start earning something ko dan future din yayan nan. 28 4 9:19 PM Amma Sa'adatu taki "in na gama takaba zamu zauna da family dinsa na Katsina, akwai gidaje da yawa yana da su, akwai sauran kadarori, idan an raba an bamu namu sai mu shiga kasuwar da su. Yanzu ke zaki biya wa yaran kudin makaranta, ki kuma bamu abinda zamu rike a hannun mu kafin komai ya warware. And that was what happened, Safiya ce ta saka musu furnitures da komai a gidan da suka yi renting din sannan ta ajiye musu kayan abinci ta kuma biya kudin makaranta sannan ta basu kudin kashewa. Ba haka ta so ba. Ba wai dan bata son yi din ba sai dan tana son Sa'adatu ta fahimci situation din da take ciki a yanzu, she have been there, she knows the probable outcome. Ai kam dai sanda aka raba gadon Alhaji Ibrahim sam abinda Sa'adatu ta saka ran zata samu ba shi ta samu ba daga ita har yaran. Sunce suma efcc ta kwace da yawa daga abinda yake hannun su, a cikin abinda ya rage gida kadai suka samu ita da yayanta a Katsina. And the first thing da tayi tun kafin ma ta gaya wa kowa abinda ta samu shine ta saka gidan a kasuwa ta siyar. Sanda Hajiya taji ba karamin fada tayi mata ba "kina da kananan yaya ciki har da namiji amma ki siyar musu da gidan gadon su? Ba zaki bar shi yayi musu amfani nan gaba ba?" Tace "to Hajiya idan ban siyar ba da me zan rike su? Kudin da zan siya mana kayan abinci ma fa bani da shi" Hadiya tace "ki dauko su ku dawo nan gidan ku zauna kinga baku da matsalar abinci kenan. Zan baki jari kuma ki fara sana'a. Kudin gidan da kika siyar kuma ki sayi ko wani ne acan da ba zai siya miki gida anan ba, ko kuma fili, ko ki sayi gold ki ajiye, amma whatever you do kar ki kashe su". Sai dai wanna hukuncin bai yiwa Sa'adatu dadi ba. Sam bata son zaman gidan Hajiya gani take tafi karfin haka a yanzu. Kuma abinda ya kara koma mata rai shine ire yaran da Hajiya ta yi daga makarantar da suke zuwa mai dan karen tsada ta dawo dasu wacce zata iya biya musu. Ita Sa'adatu gani take yi abin kunya ne kawayen ta suga tana zaune a gidan su kuma yayanta suka karamar makaranta. She went to Safiya for help amma Safiya tace ba zata iya tsallake abinda Hajiya tace ba. "Tunda ta cire su daga makarantar idan na mayar da su nayi mata ba dai dai ba. Kiyi hakuri, watarana ke da kanki zaki mayar da su. Yanzu ki kawo kudin hannunki akwai wata dama da zata shigo min kwanan nan sai in saka kudin naki a ciki, ki basu kamar shekaru uku kadai ki gani yadda kudin zasu zama. Ko kuma kiyi daya daga cikin shawarwarin da Hajiya ta baki", Amma Sa'adatu ba tayi haka ba. Sai ta bar kudin a cikin account dinta "for security purposes, zama babu kudi a hannu kudin a cikin account dinta "for security purposes, zama babu kudi a hannu tsautsayi ne", And a year later ko kwandala babu a cikin kudin. Safiya da Hajiya sun bawa Sa'adatu jari iya adadin da su kansu basu san yawan saba, amma da sun bata an kwana biyu za ta ga babu shi babu alamun sa, kudi kamar ta tsakanin yatsun hannunta ta yake wucewa, bata taba koyon yadda zata hade yatsun ta hana kudin fita ba. Akwai lokacin da Safiya ta bata wasu kudi sai ta mayar mata da su tace "ki juya min su ke da kanki. Kiyi min abinda kika yiwa kanki. Ni ribar kawai zaki ke bani ki rike E3 war" safiya tayi dariya tana mamakin halin Sa'adatu tace "ranar da bana duniya kuma fa? Waye zai juya miki ya baki ribar kawai. Dole sai kin koya. Nobody will take care of you except you". Amma Sa'adatu a ranta ta san wanda zai kula da ita da yayanta. Ta san abinda take bukata. Wani mijin take bukata mai kudin da zai rike ta ita da yayanta. She was not born to suffer like this. She was not born to take care of herself and her children. She was born to be taken care of, Present days...…. "Fiyya?" Naji an kira sunana kamar daga sama. Na dauke idona daga kan fuskar mahaifiyata na juyo na kalli mai kiran sunana, Mommy ce. Tace "me kike yi ne ke kadai a zaune kamar gunki?" Sai kuma ta kalli hoton da ta lura shi nake kallo, tai ajjiyar zuciya ta karaso cikin dakin ta zauna a bakin dago tana cigaba da kallon hoton tace "I miss her too.... .. She was so smart. 21 12 3 9:19 PM The smartest human being I have ever seen" ta danyi murmushi "na taba tambayar ta cewa anya kuwa ba da aljanu take aiki ba? Cos she will be like "Sa'adatu idan kika yi this, this and that ne zai faru amma idan kika yi that, that and that ne zai faru" and abinda duk ta fada din shine abinda yake faruwa sai dan banbanci kadan, and then she will be like "I told you so, ba kya jin magana Sa'adatu" Ta danyi dariya sai kuma muka cigaba da yin shiru awkwardly, Ganin dai still bani da niyyar yin magana sai ta sake cewa '"dama zuwa nayi in taya ki hada kayan ki. Kin san gobe zamu tafi. Gwara in shirya miki kayan ki tun yanzu" na dan yi gyaran murya sannan nace "thank you Mommy, Esther ta gama hada min ai. Nagode sosa'" muka cigaba da yin shiru sannan Mommy ta mike tace "okay then. In kina bukatar wani abun dai just let me know". Da haka ta fita. Na bi bayanta da kallo har ta fita sannan na girgiza kaina a hankali nace "ki je ki hada kayan mijinki mana, me yasa ba zaki hada mishi kaya ba sai ni zaki hada wa" na yi dan karamin tsaki nace "bunch of munafukai" Na juya na cigaba da kallon hoton Ammi na. She was the smartest just like Mommy just said, and that means if she were here with me right now she will not let me sit here alone in my room crying like a coward, she would tell me to put my past behind me and take control of my future. And that is exactly what I am going to do. cannot be her, but I am going to be the daughter she would have been proud of. Kafin safe na gama yanke hukuncin duk abinda zanyi. After subh prayer ban koma bacci ba sai na zauna nayi azkar dina sannan nayi duk adduoin neman yarda Allah akan abubuwan da na saka a gaba da kuma neman guidance dinsa akan abubuwan da suka shige mun duhu, nayi wa Ammi addu'ar samun rahamar ubangiji sannan nayi wa Muhammad addu'ar Allah ya sanyaya masa zuciyarsa ya bashi ikon karbar kaddarar sa. Sai da gari ya gama wayewa sannan na tashi na shiga toilet nayi wanka, taking care kar in fama ciwona, and seeing the scar sai na tambayi kaina ko ya yake ciki? How is he? Amma kuma ni na san ba zan iya kiran Aunty Hajjo in tambaye ta shi ba. Na fito daga wanka na shiga closet dina, somewhere that I have not been in for a while, a ciki naje na bude wata wardrobe da tun da Daddy da kansa ya zuba kayan ciki ban taba bude ta ba. Partly because I was not emotionally ready. Sai dai na san kayan ciki kamar sauran kaya na are been well cared for by Esther. Na tsaya ina bin kayan da kallo tun daga sama har kasa, kayan Ammi ne, bayan rasuwar ta Daddy took duk kayan ta da yasan zasu yi lasting years har zuwa lokacin da zan iya saka su ya adana su safely, bai bani ba sai two years ago on my 20th birthday, ranar da ya gaya min maganganu da yawa da suka hargitsa rayuwa ta, And for the two years they have been with me ban taba taba su ba ballantana in saka. I doubt idan zasu yi min dai dai ma. Na saka hannu na shafa su yadda suke a jere ina jin texture din su sannan hannuna ya sauka akan wani lace cream mai laushi a hannu. Na jawo shi na fito da shi sannan na warware, duguwar riga ce da aka yi mata aiki mai kyau a wuya, simple dinki ne irin wanda nake so wanda ba zai takurawa mutum ba. Ga mamaki na material din babu abinda yayi, daga gani an kashe kudi a gurin siyan sa. Na daga kayan na kai hancina hoping ko zan ji wani scent da zsi iya tuna min da memory dinta amma banji komai ba sai kamshin wardrobe balls. Na saka undies dina sannan na saka rigar, tsahon kamar an auna da ni amma kuma wuyan ya dan yi min yawa kadan, ko dai ta fini fadi ko kuma ramar da nayi ce ta saka haka. 43 Na jawo dan karamin akwatin da yake kasa wanda Daddy ya rufe da pin, na saka 3 9 pin din na bude na tsaya ina kallon O O contents din ciki, sarkokin ta ne, sarkoki na. A jere a cikin boxes din su. Tun da ta rasu Daddy ya kai su ajjiya banki sai on my 20th birthday ya karbo su ya bani together with a lot of things. Na dauko wata na bude box din ina kallon ta, na gane ta, ita ce a wuyanta a pictures din ranar suna na. Na cire dan kunnen na saka sannan na saka sarkar ita ma. Na mike tsaye ina kallon kaina a madubi, 23 9:19 PM I looked very different from Fiyya. I looked more like Safiya. Na daura dankwalin sannan na yafa mayafina da ya shiga da kayan na rufe komai na fita. A daki na dauki jaka ta tare da key din mota ta na fita na kuma rufe kofar dakin. Ina fita muka hadu da Esther, ta tsaya tana kallona da mamaki amma bata ce komai ba, nayi mata murmushi "'ina Daddy?" Ta nuna kasa da hannun ta "he is downstairs, they are all downstairs. Shi yace in kira ki kuyi breakfast" nace "okay. Please get me my banana smoothie" tayi murmushi, ina ganin farin ciki a fuskar ta tace "yes ma'am" ta juya da sauri and I heard her say "finally!" Na gyara zaman wuyan rigar a jikina sannan na fara sauka daga stairs din a hankali, making sure cewa takalma na suna making sound, and as I expected, ina zuwa point din da zasu ganni na ga gabakidaya suna kallon side dina. A lokaci daya all their jaws dropped. Suna zaune a kan dining table, Mommy da Mustapha da Hassan da Hussaini. Daddy kuma yana zaune akan wheelchair dinsa a gefen su alone like an island. Suna cin abinci shi kuma yana karanta newspaper. Newspaper din ta zame daga hannun sa ta fadi akan cinyarsa. Hassan yace "woW" Hussain yace "masha Allah" Mommy tace "dama sarkar nan tana nan?" Na wuce su dukkan su na tafi gaban Daddy da har lokacin ya kasa furta komai. Na durkusa a gaban sa fuska ta da murmushi nace "good morning Daddy" sai kuma na dago na yi kissing cheeks dinsa kamar yadda nake yi sanda ina yarinya. A lokacin Esther tazo da smoothie na a dogon mug ta miko min. Hassan yace "the smoothie is back!" Nayi murmushi tare da daga masa cup din nace "yes dear, I am back" sai kuma na gaishe da Mommy da tun da ta mike tsaye sanda na shigo bata zauna ba. Ta amsa har lokacin da mamaki a fuskarta tace "you look a lot like her" nayi murmushi "thank you"., Sai kuma na juya na gaishe da Mustapha da yake ta jujuya cokalin hannunsa tunda na shigo, Na jawo kujera kusa da Daddy na zauna, har lokacin kallo na yake, na fara shan smoothie na still ina cigaba da bin mutanen gurin da kallo, har lokacin dai kallo na suke yi. Na yi musu murmushi daya bayan daya, sai da na shanye abin da yake cikin cup din tas sannan na ajiye na juya ina kallon Daddy nace "Daddy ina son magana da kai, and it is important" ya yi ajjiyar zuciya yace "she wore that necklace ranar sunan ki" nayi murmushi tare da rike hannunsa, ya sake cewa "thank you for wearing it" na sauke ido na kasa ina kallon hannunsa nace "thank you for keeping it" yayi murmushi for the first time tunda na shigo gurin sannan yace "wacce magana ce zamu y" na dan daga £3 murya dan ina son kowa yaji abinda zance nace "dan ka amince Daddy, I want to take over" his smile brightened, na san ya fahimci abinda nake nufi amma sai ya sake tambaya, maybe to make sure "take over what?" Nace "take over every thing" and I saw farinciki a idonsa, na cigaba "in ka amince I want you to call Uncle Ahmad da duk wani wanda wani abu yake hannun sa, saboda su fara preparing everything, I want to take over as soon as possible" ya cigaba da murmushi "good, very good" Mommy tace "finally! Kai amma naji dadin wannan labarin. Na gaji da mulkin da Ahmad yake mana dama a gidan nan, komai muke so sai mun tambaye shi kamar kudin sa" ban ce komai ba na mike na ajiye cup din hannuna akan table din a gaban Mustapha, Hassan yana cigaba da kallo na yace "kinyi kyau sosai yaya" nace "'tukunna ma Hassan" na juya ina kallon Mommy nace "Mommy zan dan fita please" tayi murmushi, daga alama taji dadin tambayarta da nayi tace "ina zaki je? Kin san dai in an jima zamu tafi ko?" Nace "zan je gyaran jiki ne, ina son in wanke kaina in kuma yi manicure and pedicure, flight din ai sai yamma" tace "kiyi dai a hankali, kin san ciwon ki bai warke ba" na gyada kai kawai, a raina ina tuna cewa Ammi bata hakura ta zauna a guri daya tana kuka ba, she walked barefooted many kilometers da ciwo a kafar ta dan tayi securing good future for me. O 21 12 9 9:19 PM Na dauki jaka ta da car keys dina nayi hanyar waje, sai da na kai bakin kofa na juyo, har lokacin ni suke kallo, sai na fadi abinda nayi tunanin Daddy zai yi retaliating to, ina sane na bar maganar a 293 Marshe "na manta Daddy, also want to re-open The Oasis. In kin amince" nayi shiru ina jiran no daga gare shi, but he kept on smiling and said "good luck" Maman Maama✍🏻[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA❤️‍🩹 Episode Thirty Three : The Oasis (U 6 Paid Advert Yar uwa kinsan illar dake tareda infection kuwa,to bari kiji kadan daga cikin illar da infection yake da ita, kinsan cewa infection yana hana haihuwa,yana hana ma'aurata jindadin mu amala,yanasa warin gaba kowane irin tirare kika sa bazai hana wannan warin fita daga jikin kiba fitar farun ruwa kaikayin gaba tusar gaba duk suna daga cikin illar da infection yakewa Ifyr ki. Ina masu fama da ulcer, Asthma,sickle, ina matar dake fama da fibriod, matsalar rashin haihuwa ko bushewar jiki da fata haddake mai son hibs da breas ina uwar gida maison faranta ran oga a othe room kema ba abarkiba jawarawa da yanmata ku garzayo kuma ku kwada ku gani munada feminine wash,garlic oil da dai sauransu munada VIP chair akwai blood circulatory machine ga kuma data1g250 cikin sauki da rankwame da rahusa kedai kira number nan domin karin bayani 07035275119, 08038098317 Adam yayi shiru yana kallon ta yana kuma nazarin maganganun ta, a karshe sai yace "you can gift dukiyar ki to her, but you cannot give a will na cewa idan ta mutu kafin ta samu yaya a kai dukiya charity, it is not islamically possible. In dai kin bata then you no longer have the right to dictate yadda zata yi da ita. Zata iya duk abinda ta ga dama da ita. And ko da ita din ma, bata da damar cewa ga abinda za"a yi da dukiyar in ta mutu, tana dai da damar tayi abinda taga damar yi da ita idan tana da rai, kamar yadda ke ma yanzu zaki yi abinda kika ga damar yi da ita yanzu da kike da rai". Tayi shiru tana tunani, ta san cewa gaskiya ya fada, ta dago kai tana kallon sa, she still had that stubborn look a tare da ita "bana son ta zama target na mutane saboda dukiyar ta, bama so mutane su cutar da ita saboda dukiyar ta. In haka ta faru na zalunce ta" ta danyi shiru sai kuma tace "I will still sign the contract" yace "how? Zaki ketare iyakar ubangiji kenan?" Tayi murmushi "no. I will forge the contract. Zamu gayawa mutane cewa munyi agreement da lawyers din da suke kula da dukiyar cewa zasu bayar da ita ga charity idan Safiyya ta rasa ranta kafin ta haihu. We will make them think and believe that. While in reality ba zamuyi hakan ba. We will make them take care of her ko dan su amfana da dukiyar ta, knowing idan wani abu ya same ta zasu rasa both ita and the money", Adam yace "I don't know why you are saying "they', Mu zamu kula da yar mu and we will raise her together. Su kuma wadanda kika yi haka saboda will never get close to har ballantana har su kula da ita. Ban fahimci suwa kike nufi ba" tace "every body. In nace 'they' ina nufin everyone. Akan issue din Fiyya da dukiyar nan ban yarda da kowa ba sai kai sai Hajiya. Ko Sa'adatu ban yarda da ita ba, ban yarda da yan'uwan ka ba, ban yarda da duk wanda zai zo kusa da ita ba. Ba wai cewa nayi su ba mutanen kirki ba ne ba, but money can change people or sometimes it brings out their true color. It can corrupt even the most purest of hearts sai wanda Allah ya kare. Yana daga cikin challenges da masu kudi suke fuskanta cewa basa iya gane wanda yake son su saboda Allah da kuma wanda yake son kudin su. Kana ganin da bani da kudin nan yan'uwanka zasu yi shiru a lokacin da nayi shekaru goma sha biyar a gidan ka ba tare da na haihu ba? Har kuma su dauki babyn da suka haifa suce sun bani kyauta?" ya yi kokarin defending dan uwansa "Ahmad have been managing businesses din mu for ears, bamu taba samun matsala ba" tace "saboda akwai masu monitoring shige da fice da kudi. Ka fahimce ni, ba nace ina zargin Ahmad ba ko kuma nace shi ba mutumin kirki ba ne ba, am just saying kudi most of the times shaidan ne. It can corrupt him. Musamman yanzu idan za'a yi wannan transfer of ownership din dole zai sani saboda yana managing bangarori da yawa na dukiyar. 20 14 9:19 PM Ahmad bashi da gado na but in na bawa Fiyya na matso da kudin toward him, I want him to believe idan wani abu ya same ta nobody is getting anything, I want everyone that will ever come close to her to believe that, ko nan gaba zaka yi aure zaka haifi wasu yayan I want the wife and the children to believe that, ko ta girma zata yi aure I want the husband to believe that". Adam ya dafe kansa yana jin yana sara masa, shi kansa duk ciwo yake yi masa with all these lissafi marar tishe da take yi. She is alive and well, babu amfanin wadannan lissafe lissafen, Yace "Okay, please stop talking as if kina bankwana da duniya ne, kina saka wa ina kasa gane komai. You have been talking and now it is time for me to respond. Macanar for you to have a peace of mind cewa mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba. And maganar charity bla bla bla, shima zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar gaskiya zaki yi signing ba. But magana daya zan kara akai, Koma me kika yi I do not want Fiyya to know. I want her to have a normal childhood and grow up to be stronger than even you. I don't want her to grow up with this burden on her shoulders. Har sai ta girma ta mallakin hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda zata kula da kyautar da kika yi mata sannan zata sani. If you agree to this than everything else is fine with me". And that was how the agreement was concluded and within months aka gama komai. Everything da Safiyya ta mallaka wanda yake da takardar shaidar mallaka sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya Adam Muhammad. Tun daga kan shares dinta in factories din su ita da Adam har kan wadanda take da outsiders, har aka sauko kan personal belongings dinta su sarkokin ta da motocin ta and every other valuable possession, Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a lokacin ya sani, kamar yadda kuma a gabansa tayi signing takardar bogin da ta komai. You have been talking and now it is time for me to respond. Maganar transfer of ownership na yarda kiyi, just for you to have a peace of mind cewa mutanen Kura ba zasu karbi kudin nan ba. And maganar charity bla bla bla, shima zaki iya yi tunda kince ba yarjejeniyar gaskiya zaki yi signing ba. But magana daya zan kara akai. Koma me kika vi I do not want Fiyya to know. I want her to have a normal childhood and grow up to be stronger than even you. I don't want her to grow up with this burden on her shoulders. Har sai ta girma ta mallakin hankalin kanta ta kuma samu ilimin yadda zata kula da kyautar da kika yi mata sannan zata sani. If you agree to this than everything else is fine with me" And that was how the agreement was concluded and within months aka gama komai. Everything da Safiyya ta mallaka wanda yake da takardar shaidar mallaka sai da aka chanja sunan ya koma Safiyya Adam Muhammad. Tun daga kan shares dinta in factories din su ita da Adam har kan wadanda take da outsiders, har aka sauko kan personal belongings dinta su sarkokin ta da motocin ta and every other valuable possession, Da Ahmad akayi komai, dan haka tun a lokacin ya sani, kamar yadda kuma a gabansa tayi signing takardar bogin da ta rubuta da kanta cewa if anything is to happen to Safiyya Adam Muhammad komai in her name will go to charity. And after doing all that, Safiya became happier and more relaxed. Ta mayar da hankalinta kachokam kan kula da jaririyar yar ta wadda tafi so fiye da rayuwar ta. A cikin watannin ne kuma kaddara ta saukar wa Sa'adatu. Mijinta uban yayan ta yayi accident ya mutu. Wannan mutuwa ba karamin daga hankalin Sa'adatu da duk wanda yake tare da ita tayi ba. Ya tafi ya barta da 8 years old Mustapha and 2 years old Safina. And Safiya was there for her, a kan kafadun ta Sa'adatu tayi kukan rashin mijinta, a gidan ta kuma tayi spending most of her moaning period. Sai dai kuma tun kafin ta fita daga takaba efcc suka dira a gidan ta suka kore su daga ciki suka garkame gidan da sunan yana under investigation. Sannan kuma suka yi freezing account din mijin. Shawarar da Safiya ta fara bata sanda tazo gidan ta tana kuka tana gaya mata abinda ya far shine ta koma gidan Hajiya ita da yaran for the mean time kafin a warware problem din amma Sa'adatu ta girgiza kanta "ba zan iya komawa gidan Hajiya ba, ga yara" Safiya tace "me zai hana? Hajiya tana rike wadanda bata da hadi da su ma ballantana su Mustapha da suke kamar jikoki a wajenta" Sa'adatu ta sake girgiza kai "duk wanda ya riga ya wuce age din zama a gida ya riga ya wuce. Ina komawa raini ne zai shiga tsakani na da mutanen da suke gidan" Safiya tace "to ki zauna anan, akwai isassun dakunan da ba zaku takura ba daga ke har yara" shima Sa'adatu ta ki yarda tace "ba zan zo in zauna miki a gida ba ga mijinki yana gidan". A karshe sai ta tattara kudin duk da take da shi a account dinta ta kama rent din gida a nan Abuja duk kuwa da yadda Safiya ta nuna kin amincewar ta da maganar. "In kika karar da kudin hannunki akan rent da me kuma zaki biya wa yara kudin makaranta da me kuma zaki cigaba da rayuwa? Wannan kudin da hannun ki kamata yayi ki juya shi, this is the right time to fold up your sleeves and start earning something ko dan future din yayan nan. 28 4 9:19 PM Amma Sa'adatu taki "in na gama takaba zamu zauna da family dinsa na Katsina, akwai gidaje da yawa yana da su, akwai sauran kadarori, idan an raba an bamu namu sai mu shiga kasuwar da su. Yanzu ke zaki biya wa yaran kudin makaranta, ki kuma bamu abinda zamu rike a hannun mu kafin komai ya warware. And that was what happened, Safiya ce ta saka musu furnitures da komai a gidan da suka yi renting din sannan ta ajiye musu kayan abinci ta kuma biya kudin makaranta sannan ta basu kudin kashewa. Ba haka ta so ba. Ba wai dan bata son yi din ba sai dan tana son Sa'adatu ta fahimci situation din da take ciki a yanzu, she have been there, she knows the probable outcome. Ai kam dai sanda aka raba gadon Alhaji Ibrahim sam abinda Sa'adatu ta saka ran zata samu ba shi ta samu ba daga ita har yaran. Sunce suma efcc ta kwace da yawa daga abinda yake hannun su, a cikin abinda ya rage gida kadai suka samu ita da yayanta a Katsina. And the first thing da tayi tun kafin ma ta gaya wa kowa abinda ta samu shine ta saka gidan a kasuwa ta siyar. Sanda Hajiya taji ba karamin fada tayi mata ba "kina da kananan yaya ciki har da namiji amma ki siyar musu da gidan gadon su? Ba zaki bar shi yayi musu amfani nan gaba ba?" Tace "to Hajiya idan ban siyar ba da me zan rike su? Kudin da zan siya mana kayan abinci ma fa bani da shi" Hadiya tace "ki dauko su ku dawo nan gidan ku zauna kinga baku da matsalar abinci kenan. Zan baki jari kuma ki fara sana'a. Kudin gidan da kika siyar kuma ki sayi ko wani ne acan da ba zai siya miki gida anan ba, ko kuma fili, ko ki sayi gold ki ajiye, amma whatever you do kar ki kashe su". Sai dai wanna hukuncin bai yiwa Sa'adatu dadi ba. Sam bata son zaman gidan Hajiya gani take tafi karfin haka a yanzu. Kuma abinda ya kara koma mata rai shine ire yaran da Hajiya ta yi daga makarantar da suke zuwa mai dan karen tsada ta dawo dasu wacce zata iya biya musu. Ita Sa'adatu gani take yi abin kunya ne kawayen ta suga tana zaune a gidan su kuma yayanta suka karamar makaranta. She went to Safiya for help amma Safiya tace ba zata iya tsallake abinda Hajiya tace ba. "Tunda ta cire su daga makarantar idan na mayar da su nayi mata ba dai dai ba. Kiyi hakuri, watarana ke da kanki zaki mayar da su. Yanzu ki kawo kudin hannunki akwai wata dama da zata shigo min kwanan nan sai in saka kudin naki a ciki, ki basu kamar shekaru uku kadai ki gani yadda kudin zasu zama. Ko kuma kiyi daya daga cikin shawarwarin da Hajiya ta baki", Amma Sa'adatu ba tayi haka ba. Sai ta bar kudin a cikin account dinta "for security purposes, zama babu kudi a hannu kudin a cikin account dinta "for security purposes, zama babu kudi a hannu tsautsayi ne", And a year later ko kwandala babu a cikin kudin. Safiya da Hajiya sun bawa Sa'adatu jari iya adadin da su kansu basu san yawan saba, amma da sun bata an kwana biyu za ta ga babu shi babu alamun sa, kudi kamar ta tsakanin yatsun hannunta ta yake wucewa, bata taba koyon yadda zata hade yatsun ta hana kudin fita ba. Akwai lokacin da Safiya ta bata wasu kudi sai ta mayar mata da su tace "ki juya min su ke da kanki. Kiyi min abinda kika yiwa kanki. Ni ribar kawai zaki ke bani ki rike E3 war" safiya tayi dariya tana mamakin halin Sa'adatu tace "ranar da bana duniya kuma fa? Waye zai juya miki ya baki ribar kawai. Dole sai kin koya. Nobody will take care of you except you". Amma Sa'adatu a ranta ta san wanda zai kula da ita da yayanta. Ta san abinda take bukata. Wani mijin take bukata mai kudin da zai rike ta ita da yayanta. She was not born to suffer like this. She was not born to take care of herself and her children. She was born to be taken care of, Present days...…. "Fiyya?" Naji an kira sunana kamar daga sama. Na dauke idona daga kan fuskar mahaifiyata na juyo na kalli mai kiran sunana, Mommy ce. Tace "me kike yi ne ke kadai a zaune kamar gunki?" Sai kuma ta kalli hoton da ta lura shi nake kallo, tai ajjiyar zuciya ta karaso cikin dakin ta zauna a bakin dago tana cigaba da kallon hoton tace "I miss her too.... .. She was so smart. 21 12 3 9:19 PM The smartest human being I have ever seen" ta danyi murmushi "na taba tambayar ta cewa anya kuwa ba da aljanu take aiki ba? Cos she will be like "Sa'adatu idan kika yi this, this and that ne zai faru amma idan kika yi that, that and that ne zai faru" and abinda duk ta fada din shine abinda yake faruwa sai dan banbanci kadan, and then she will be like "I told you so, ba kya jin magana Sa'adatu" Ta danyi dariya sai kuma muka cigaba da yin shiru awkwardly, Ganin dai still bani da niyyar yin magana sai ta sake cewa '"dama zuwa nayi in taya ki hada kayan ki. Kin san gobe zamu tafi. Gwara in shirya miki kayan ki tun yanzu" na dan yi gyaran murya sannan nace "thank you Mommy, Esther ta gama hada min ai. Nagode sosa'" muka cigaba da yin shiru sannan Mommy ta mike tace "okay then. In kina bukatar wani abun dai just let me know". Da haka ta fita. Na bi bayanta da kallo har ta fita sannan na girgiza kaina a hankali nace "ki je ki hada kayan mijinki mana, me yasa ba zaki hada mishi kaya ba sai ni zaki hada wa" na yi dan karamin tsaki nace "bunch of munafukai" Na juya na cigaba da kallon hoton Ammi na. She was the smartest just like Mommy just said, and that means if she were here with me right now she will not let me sit here alone in my room crying like a coward, she would tell me to put my past behind me and take control of my future. And that is exactly what I am going to do. cannot be her, but I am going to be the daughter she would have been proud of. Kafin safe na gama yanke hukuncin duk abinda zanyi. After subh prayer ban koma bacci ba sai na zauna nayi azkar dina sannan nayi duk adduoin neman yarda Allah akan abubuwan da na saka a gaba da kuma neman guidance dinsa akan abubuwan da suka shige mun duhu, nayi wa Ammi addu'ar samun rahamar ubangiji sannan nayi wa Muhammad addu'ar Allah ya sanyaya masa zuciyarsa ya bashi ikon karbar kaddarar sa. Sai da gari ya gama wayewa sannan na tashi na shiga toilet nayi wanka, taking care kar in fama ciwona, and seeing the scar sai na tambayi kaina ko ya yake ciki? How is he? Amma kuma ni na san ba zan iya kiran Aunty Hajjo in tambaye ta shi ba. Na fito daga wanka na shiga closet dina, somewhere that I have not been in for a while, a ciki naje na bude wata wardrobe da tun da Daddy da kansa ya zuba kayan ciki ban taba bude ta ba. Partly because I was not emotionally ready. Sai dai na san kayan ciki kamar sauran kaya na are been well cared for by Esther. Na tsaya ina bin kayan da kallo tun daga sama har kasa, kayan Ammi ne, bayan rasuwar ta Daddy took duk kayan ta da yasan zasu yi lasting years har zuwa lokacin da zan iya saka su ya adana su safely, bai bani ba sai two years ago on my 20th birthday, ranar da ya gaya min maganganu da yawa da suka hargitsa rayuwa ta, And for the two years they have been with me ban taba taba su ba ballantana in saka. I doubt idan zasu yi min dai dai ma. Na saka hannu na shafa su yadda suke a jere ina jin texture din su sannan hannuna ya sauka akan wani lace cream mai laushi a hannu. Na jawo shi na fito da shi sannan na warware, duguwar riga ce da aka yi mata aiki mai kyau a wuya, simple dinki ne irin wanda nake so wanda ba zai takurawa mutum ba. Ga mamaki na material din babu abinda yayi, daga gani an kashe kudi a gurin siyan sa. Na daga kayan na kai hancina hoping ko zan ji wani scent da zsi iya tuna min da memory dinta amma banji komai ba sai kamshin wardrobe balls. Na saka undies dina sannan na saka rigar, tsahon kamar an auna da ni amma kuma wuyan ya dan yi min yawa kadan, ko dai ta fini fadi ko kuma ramar da nayi ce ta saka haka. 43 Na jawo dan karamin akwatin da yake kasa wanda Daddy ya rufe da pin, na saka 3 9 pin din na bude na tsaya ina kallon O O contents din ciki, sarkokin ta ne, sarkoki na. A jere a cikin boxes din su. Tun da ta rasu Daddy ya kai su ajjiya banki sai on my 20th birthday ya karbo su ya bani together with a lot of things. Na dauko wata na bude box din ina kallon ta, na gane ta, ita ce a wuyanta a pictures din ranar suna na. Na cire dan kunnen na saka sannan na saka sarkar ita ma. Na mike tsaye ina kallon kaina a madubi, 23 9:19 PM I looked very different from Fiyya. I looked more like Safiya. Na daura dankwalin sannan na yafa mayafina da ya shiga da kayan na rufe komai na fita. A daki na dauki jaka ta tare da key din mota ta na fita na kuma rufe kofar dakin. Ina fita muka hadu da Esther, ta tsaya tana kallona da mamaki amma bata ce komai ba, nayi mata murmushi "'ina Daddy?" Ta nuna kasa da hannun ta "he is downstairs, they are all downstairs. Shi yace in kira ki kuyi breakfast" nace "okay. Please get me my banana smoothie" tayi murmushi, ina ganin farin ciki a fuskar ta tace "yes ma'am" ta juya da sauri and I heard her say "finally!" Na gyara zaman wuyan rigar a jikina sannan na fara sauka daga stairs din a hankali, making sure cewa takalma na suna making sound, and as I expected, ina zuwa point din da zasu ganni na ga gabakidaya suna kallon side dina. A lokaci daya all their jaws dropped. Suna zaune a kan dining table, Mommy da Mustapha da Hassan da Hussaini. Daddy kuma yana zaune akan wheelchair dinsa a gefen su alone like an island. Suna cin abinci shi kuma yana karanta newspaper. Newspaper din ta zame daga hannun sa ta fadi akan cinyarsa. Hassan yace "woW" Hussain yace "masha Allah" Mommy tace "dama sarkar nan tana nan?" Na wuce su dukkan su na tafi gaban Daddy da har lokacin ya kasa furta komai. Na durkusa a gaban sa fuska ta da murmushi nace "good morning Daddy" sai kuma na dago na yi kissing cheeks dinsa kamar yadda nake yi sanda ina yarinya. A lokacin Esther tazo da smoothie na a dogon mug ta miko min. Hassan yace "the smoothie is back!" Nayi murmushi tare da daga masa cup din nace "yes dear, I am back" sai kuma na gaishe da Mommy da tun da ta mike tsaye sanda na shigo bata zauna ba. Ta amsa har lokacin da mamaki a fuskarta tace "you look a lot like her" nayi murmushi "thank you"., Sai kuma na juya na gaishe da Mustapha da yake ta jujuya cokalin hannunsa tunda na shigo, Na jawo kujera kusa da Daddy na zauna, har lokacin kallo na yake, na fara shan smoothie na still ina cigaba da bin mutanen gurin da kallo, har lokacin dai kallo na suke yi. Na yi musu murmushi daya bayan daya, sai da na shanye abin da yake cikin cup din tas sannan na ajiye na juya ina kallon Daddy nace "Daddy ina son magana da kai, and it is important" ya yi ajjiyar zuciya yace "she wore that necklace ranar sunan ki" nayi murmushi tare da rike hannunsa, ya sake cewa "thank you for wearing it" na sauke ido na kasa ina kallon hannunsa nace "thank you for keeping it" yayi murmushi for the first time tunda na shigo gurin sannan yace "wacce magana ce zamu y" na dan daga £3 murya dan ina son kowa yaji abinda zance nace "dan ka amince Daddy, I want to take over" his smile brightened, na san ya fahimci abinda nake nufi amma sai ya sake tambaya, maybe to make sure "take over what?" Nace "take over every thing" and I saw farinciki a idonsa, na cigaba "in ka amince I want you to call Uncle Ahmad da duk wani wanda wani abu yake hannun sa, saboda su fara preparing everything, I want to take over as soon as possible" ya cigaba da murmushi "good, very good" Mommy tace "finally! Kai amma naji dadin wannan labarin. Na gaji da mulkin da Ahmad yake mana dama a gidan nan, komai muke so sai mun tambaye shi kamar kudin sa" ban ce komai ba na mike na ajiye cup din hannuna akan table din a gaban Mustapha, Hassan yana cigaba da kallo na yace "kinyi kyau sosai yaya" nace "'tukunna ma Hassan" na juya ina kallon Mommy nace "Mommy zan dan fita please" tayi murmushi, daga alama taji dadin tambayarta da nayi tace "ina zaki je? Kin san dai in an jima zamu tafi ko?" Nace "zan je gyaran jiki ne, ina son in wanke kaina in kuma yi manicure and pedicure, flight din ai sai yamma" tace "kiyi dai a hankali, kin san ciwon ki bai warke ba" na gyada kai kawai, a raina ina tuna cewa Ammi bata hakura ta zauna a guri daya tana kuka ba, she walked barefooted many kilometers da ciwo a kafar ta dan tayi securing good future for me. O 21 12 9 9:19 PM Na dauki jaka ta da car keys dina nayi hanyar waje, sai da na kai bakin kofa na juyo, har lokacin ni suke kallo, sai na fadi abinda nayi tunanin Daddy zai yi retaliating to, ina sane na bar maganar a 293 Marshe "na manta Daddy, also want to re-open The Oasis. In kin amince" nayi shiru ina jiran no daga gare shi, but he kept on smiling and said "good luck" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Thirty Four: The Oasis 2 Na shiga mota ta na tayar, sannan na dauko sunglasses din da nakan ajiye a cikin motar na saka a idona, remembering cewa the last time da na shiga cikin ta shine ranar da naje office din Muhammad. Nayi saurin kawar da tunanin sa daga zuciyata, tun jiya da na gama deciding to be strong na fahimci cewa shine kadai zai zamo weakness dina, babban kuma makamin da zanyi amfani da shi in yaki wannan weakness din shine inyi nesa da shi. Wannan yasa na kuma tabbatar wa da kaina cewa tafiya Kano tare da Daddy shine alkhairi a gare ni a yanzu. But before that I need to go to the oasis, I need to see it, Na san a inda yake, duk kuwa da cewa sai daya na taba zuwa gurin da wayo na, shima kuma Uncle Ahmad ne ya taba kaimu ni da Mustapha da Safina wani zuwa da muka taba yi Abuja hutu gidan sa. Shima kuma bamu dade a ciki ba ya dauke mu muka fita saboda lokacin gurin a cike yake da ciyawa. A lokacin ban san menene gurin ba, ban kuma san me ya faru a gurin ba. Na kara gudun motar dan gurin da dan nisa kuma bana so lokaci ya kure ban dawo gida ba ran Daddy ya baci, a haka har na karasa unguwar da gidan gonar yake. It looks more congested then I can remember. Wannan ya sa hanyar ta bace min har sai da na fito daga motar nayi ta tambaya "dan Allah wani tsohon gidan gona nake nema anan unguwar yake" sai dai mutane da yawa basu gane ba, sai na fahimci yanzu it is no longer gidan gona dan haka mutane da yawa ba zasu sanshi a matsayin gidan gona ba. Sai da kyar na samu wani mai babur din haya yace ya san gurin, ya tafi gaba na bishi a baya har muka bar cikin gidajen mutane sannan muka fito wani filin ball sannan na hango gidan gonar. Na sallami mai babur din na karasa nayi packing na fito na tsaya ina kallon gate din, it looked old and rusty, it looked like an jima ba'a bude ta ba dan har kasa ta taru a kasa, except for karamar kofar da naga a bude take ma. Karafunan da aka saka a saman gate din in shape of the alphabets THE OASIS duk sun kakkarye wadansu ma babu su a gurin, and my bet is yan gwangwan ne suka sace. Na tura karamar kofar a hankali na shiga, babu komai sai kukan tsuntsaye sai dai kallo daya na yiwa harabar gurin na fahimci akwai mutane a ciki, daga can bangaren da akayi dakunan ma'aikatan gurin naji kukan baby, na doshi gurin sannan na dan daga murya nayi sallama. Naji muryar namiji ya amsa min, sai kuma naga wani ya fito daga daya daga cikin dakunan biyu yana kallona yana magana "waye ?" Nayi shiru ban ce komai ba har ya sauko daga kan barandar gaban dakunan sai kuma ya tsaya yana kallona, then I saw the realization as it hits him. "Hajiya Safiya?" Maficin hannunsa saura kadan ya fadi kasa. Nayi murmushi ina jin wani stick of pride yana strengthening spine dina, ina jin 23 pride duk sanda mutane suka ce ina kama da ita, to me it is a great honor. "Hajiya Safiyya" na gyara masa, "Safiyya??" Ya fada sannan ya karasa sakin maficin hannun nasa ya rufe bakin sa da hannun, sai kuma hawaye ya fara bin fuskarsa. Na cire glass din idona na cigaba da kallon sa, ya goge hawayen idonsa "kiyi hakuri Hajiya, sannu da zuwa. Da na ganki na dauka ita ce. Sai na tuno da da, sai na tuna da yadda muke da. Allah yaji kan mahaifiyar ki Allah yayi mata rahama" Nace "Ameen" yace "bismillah Hajiya, ki shigo.…." Ya fara nuna min hanyar dakunan da ya fito daga ciki, na girgiza masa kai '"na gode, amma ba zama zanyi ba, zan dan zagaya ne kadan, ina so in ga gurin ne saboda za'a zo ayi aiki nan ba da dadewa ba, za'a cigaba da duk abinda ake yi a ciki" ya rufe bakinsa cikin farin ciki "alhamdulillah, alhamdulillah. Allah maji rokon bayinsa, Allah na gode maka. Hajiya shekara ashirin kenan da rufe gidan nan kuma shekara ta ashirin kenan ina zaune har yau ban samu wani tsayayyen aiki ba, dan ma Alhaji Ahmed yace in cigaba da zama anan da iyali na da na san zuwa yanzu ko gidan zama ba zan samu ba. Allah ya tabbatar mana da wannan magana" na wuce shi na bi hanyar da na fahimci ciki ta shiga a raina ina yaba yadda aka fitar da tsarin gurin. 22 14 2 1 10:32 PM Ya biyoni a baya yana yi min bayanin ko ina da abinda yake a gurin a da. Nayi kokarin tunowa amma ban tuno komai ba. Kafin mu gama zagayen har na gama yanke hukuncin duk changes din da zanyi da kuma abubuwan da zan kara a gurin. Bayan mun gama ne kuma na tsaya ina kallon sa nace "thank you for showing me around" ya gyada kai, "nine da godiya ranki ya dade" na danyi shiru ina kallon sa sannan nace "ina reservoir din take? Ina son ganin ta" nan take naga fuskar sa ta chanja, "Hajiya??" Ya fada da rawar murya, nayi kokarin kirkirar murmushi "'babu komai. Kawai so nake in ganta" ya ~ juya reluctantly ya fara tafiya ina binsa a baya har muka je inda katon tankin ruwan gidan yake, na daga kai ina kallon girmansa, da ruwan cikinsa ake bawa dabbobin gidan ruwa da shi kuma ake bawa shukokin gidan ruwa, na sunkuyar da kaina kasa ina kallon inda mutumin ya tsaya, a kusa da kafafuwan sa akwai wata kofa ta karfe a rufe da padlock. Kofar reservoir. Yawn bukatar ruwan gidan ya saka bayan tankin aka yi katuwar reservoir a kasa ake tara ruwa a ciki, yadda in ruwan tankin ya kare za'a ja wani daga reservoir din zuwa cikin tankin sannan a kara cika reservoir din. Na durkusa na dora hannu na akan kofar karfen da ta rufe gurin, na rufe ido na ina kokarin forcing kaina to remember. Ina so in tuno wani memory din nata, ko yaya ne, ko wannan ne. Na bude ido na na dago ina kallon mutumin da yake tsaye a kusa da ni fuskarsa cike da damuwa. "Ina key din?" Na tambaye shi, ya girgiza kai bai ce komai ba sai na sake tambaya "ina key din? Dauko min" na fada a matsayin umarni ba shawara ba. Ya tsaya kamar ba zai tafi ba sai kuma ya tafi da sauri. Na sake rufe ido na trying so hard to remember. And I can almost heard my little self calling her "Ammie. Ammieme" ya bude ido na ina murmushi. Na tuna yadda nake kiran sunan ta idan muna wasa "Ammieme" she was my best friend ko minti daya bana son yi ba'a tare da ita ba. Bayan ta haife ni she gave up alot of her ambition ta koma zama a goda tare da ni. She would tell me stories most of which ba gane wa nake yi ba, she would sing me songs most of which ita take hadawa da kanta, she would play with me kamar sa'ata, muyi wasan ni iri iri, sanda na fara way favorite wasan mu shine hide and seek, zan je in buya a bayan kujera ko wani grin inyi ta kyalkyala dariya. "Hide Ammieme" nake kiran wasan, Ita kuma idan ta buya na duba ban ganta ba sai in saka kuka in kwanta a kasa ina bori sai ta fito sai in kama ta inyi ta dariya. Babban abokin wasa na bayan Ammi shine ruwa. Lokacin ina matukar kaunar wasan ruwa, duk inda na ga ruwa sai nayi wasa da shi, in me yawa ne kuma a bude sai na shiga ciki. Sai da aka koma boye ruwa a gidan mu saboda ni, tun ina rarrafe na iya bude fridge in dauko ruwa in a bude yake in kwara wa kaina shi komai sanyin sa. Ko a cup a ka bani ruwa sai in karba in kwara a kaina ince "water!!" Duk wanda ya san ni a lokacin ya san ni da wasan ruwa. Mai gadin gidan ya dawo da sauri da key a hannun sa sannan ya durkusa a kusa da ni ya bude padlock din jikin kofar, I saw his hands shaking as he was opening it. Nace masa "thank you" sai kuma ya matsa ya tsaya a bayana, maybe tunani yake yi in yabar gurin zan fada ciki ne. Na juya ina kallon sa nace "dan bani guri dan Allah" sai da yayi dan jim kadan sannan ya tafi, so nake a bar ni ni kadai, so nake in kasance daga ni sai tunani na. Na cire lock din daga jikin kofar sannan nayi kokarin daga ta, it was so heavy that sai da na saka hannu biyu sannan na daga ta. Daga cikin kofar akwai sprina wanda ya rufe, idan ka bude kofar kuma all the way akwai hook da yake rike ta a kasa ya hana ta komawa. Na makale kofar a jikin hook din sannan na mayar da ido na cikin reservoir din ina kallon ta, it was filled with water har bakin ta. It looked dark, deep and cold. Sai naji wani chilly feeling na toro ya shige ni. She jumped inside with out a second thought so save me, she died inside. Twenty years ago... 16 9 8 10:32 PM Haihuwar Fiyya ta saka Adam da Safiyya sun kara zama closer than ever, sunyi putting duk wani not so important business din su on hold dan su samu suyi raising yar tilon yar su together. Abubuwan kuma da ba zasu iya putting on hold ba sai suka yi scheduling dinsu yadda zssu yi fitting sababbin tsare- tsaren su. A cikin tsare-tsaren akwai spending every weekend at the oasis, duk Friday evening sue tahowa basa komawa gida sai Sunday evening ko kuma ma Monday morning. Idan sunzo suna zama ne su kadai without visitors without business discussions, just enjoyments and playing with their Fiyya. And that fateful weekend shima suka z0 kamar ko yaushe, Safiya ta dauki Fiyya suka shiga ciki suka yi changing into kananan kaya yayin da Adam shi kuma yake cike da dokin zuwa yayi testing sabon dokin da ya siyo. Safiya tana ta yi masa dariyar idan ya hau zai fado tunda ba iya wa yayi ba, dan haka sai yayi deciding waje zai fita da dokin ya hau, ba zai hau a cikin gidan ba kar ya fado tayi masa dariya. And they watched as he and ma"aikatan gidan guda biyu suka fita da dokin waje suka turo gate din. Suna fita Fiyya ta sauko daga hannun Safiya ta fara gudu akan pavement din wajen "hide Ammieme, hide Ammieme" Safiya tayi dariya, ta gane wasa Fiyya take so suyi, ta bita a baya, pretending kamar ita ma gudun take yi, watching how Fiyya take kokarin tsere mata da yan kananan kafafuwanta. Tace "run run little one, don't let me catch you". Fiyya ta kara karfin gudun ta zuwa wasu shuke shuken flowers da suke a gaban su ta shige ciki tana kyalkyala dariya wai ita lallai buya tayi, Safiya tazo ta wuce gurin tana neman ta "where are you...... Don't let me catch you...." Fiyya ta cigaba da dariya ganin Safiya ta wuce ta, ita a ganinta bata san tana gurin ba. Sai da Safiya ta gama zagaye gurin sannan ta saka hannu cikin flowers din ta dauko ta. "I got you" duk suka yi dariya tare, safiya ta jefa ta sama ta cafe ta. Fiyya ta fara tutture ta har saida ta sauke ta kasa sannan ta tura ta baya tare da rufe idonta da hannayenta "hide Ammieme, hide Ammieme" Safiya ta gane me take nufi, so take ta buya ita kuma ta nemo ta, ta tafi da sauri ta buya a bayan wani dan karamin daki da ake ajiye abincin dabbobin gurin, Fiyya ta fara tafiya tana neman ta tana kiran sunan ta "Ammi . Ammieme..... ." Ta cigaba da kiran sunan kamar mai waka tana zagaye a gurin har tazo kasan tankin ruwan, a lokacin ne kuma taga reservoir din, wide open, and she saw the water. Farin ciki ya bayyana a karamar fuskarta, a hankali tace "water!!!" Sai kuma ta karasa gurin da sauri ta leka tana kallon 43 sa, sai kuma ta sunkuya tana kara leka 0? ramin gurin kamar mai auna zurfin sa, sai kuma ta saka hannu daya ta taba ruwan dan tabbatar wa cewa ruwa ne da gaske, farin ciki ya sake cika zuciyar ta, "water!!!" Ta sake fada cikin jin dadi, ga ruwa ga shi kuma babu mai hana ta wasa dashi, dan haka ta zura dukkan hannayen ta biyu ciki tana jujjuya su tana watsi da ruwan zuwa jikin ta, and as she bent over more dan taji dadin wasan, she slipped and fell inside. Safiya tana tsaye a mabuyarta tana jin muryar yarta tana kiran ta cikin waka '"Ammie, Ammieme....." Sai kuma ta ji tayi shiru, tayi murmushi tana jiran taji ta fara kuka dan trick dinta kenan in ta kasa samo ta, amma kuma sai taji shiru bata ji tayi kukan ba. She waited shiru. Nan take zuciyar ta ta gaya mata cewa Fiyya was distracted, maybe ma ta manta wasa suke. And only one thing ne zaiyi distracting Fiyya daga wannan wasan. Ruwa. And she remembered the reservoir and her heart stopped. Sai dai ta san cewa the reservoir has always been heavily closed amma bata bari wannan tunanin ya tsayar da ita ba. She got to the area a dai lokacin da Fiyya tayi leaning over, and she saw her fell into the water. She screamed and called Adam, amma kuma sai ta tuna with a sinking feeling that Adam baya cikin gidan, that su kadai ne a cikin gidan. 19 6 4 10:32 PM She could have run to the gate and call for help but she didn't. She could have run to their room ta dauko wayar ta ta kira Adam but she didn't. Ta san kowanne second daya data bata zai iya making different between life and death for her daughter. And her daughter's life is something da bata saka a kasan komai ba. She ran to the reservoir and looked inside, she saw Fiyya sinking down the clear water, her small hands and legs kicking the water, her eyes wide, her body jacking as she kept on breathing in the water. And without a second thought Safiya took a deep breath and jumped inside. Bata iya swimming ba, but she went down and grabbed her daughter. Sannan kuma ruwan yayi sama da su tare, she was relieved and terrified at the same time, terrified that she was too late, that something bad had happened to her daughter, Tayi amfani da dukkanin karfin ta ta turo Fiyya's little body waje, and she was so relieved lokacin da taga Fiyya ta fara tari tana fito da ruwa daga hancinta da bakin ta, trying to get air into her lungs. Ta fara kokarin fit da kanta daga cikin ramin, garin kokarin ne ta dafa murfin, and it got released from the hook da ya rike shi a kasa, spring din da yake jikinsa ta ciki ya jawo shi da karfi. It went swiftly and heavily, and hit her on the head. She was sanda murfin ya taho kanta, and she knew she was going to die. Her life flashed before her eyes and ga mamakin ta sai taga bata da regrets, amma kuma tana burika masu yawa, babban unfulfilled wish dinta shine na ganin yarta ta girma ta samu rayuwa mai kyawun da take yi mata fata. And as the metal hit her head, just before she lost consciousness, she wondered what her daughter's life would be without her, and she prayed for God to be with her. As she lose consciousness, she sank to the bottom of the reservoir yayin da murfin ya rufe ta a ciki, the drawn. She died Twenty years later.….. Present days.....…. Na saka hannuna daya cikin ruwan ina wasa da shi tare da kokarin jera numfashi dan kawar da abinda ya toshe min makogwaro, dan hana kaina kuka kamar yadda nayi alkawari. "She drawn" na fada wa kaina a hankali, trying to console myself. "She drawn" na sake fada. "Shahada tayi, She is in Janna". Na sake jera wadansu numfarfashin sannan na mike tsaye ina kallon reflection dina a cikin ruwan. A hankali nace "rest in peace mother. Rest in peace legend". I was all emotional when I left the farm house, amma hakan bai hana ni zuwa saloon din da nace zanje ba. Nayi wa kaina alkawarin not letting me emotions get the hold of me. Saloon din da na saba zuwa ne and they gave me the special treatment da suka saba bani, naji kunya sanda aka wanke min kaina saboda irin dattin da yayi amma ana gama wa naji iska tana shiga ta ta ko'ina, aka gama min komai na fita, feeling as fresh as ever. Ban koma gida ba sai da na biya ta shagon da na saba siyayyar kayan skin care dina, and I bought all abubuwan da nake using before and more. Na riga na daura niyya kuma babu gudu babu ja da baya. Ina komawa gida nayi sallah sannan nayi joining su Mommy muka ci lunch tare. Abinda ta fara tambaya ta shine "wai dama sarkar nan tana gurin ki?" Nayi kamar ban fahimci abinda take nufi ba nace "acce sarka kenan Mommy?" Tace '"wannan ta wuyan ki. Sarkar Safiya ce. I thought Daddyn ku ya siyar da ita or something all those years ago. I was surprised to see it with you today" na ajiye spoon dina na gaya mata gaskiyar lamarin. "Bai siyar ba, ya ajiye ne a banki. Sai two years ago ya dauko su ya bani. Suna nan a dakina. Ban taba buda su ba sai yau" ta bude baki tana kallona da mamaki, sai kuma rage yayi replacing mamakin" I cannot believe it. I cannot believe Adam yana boye min maganganu irin wadannan. Ke ma kuma kina boye min maganganu irin wadannan. Me zanyi da sarkokin idan kun gaya min suna nan? But at least ya kamata ace na sani. Wannan boye boyen yafi komai bata min rai a lamarin ku. Misali yanzu tunda kuka dawo babu wanda ya gaya min ina babyn nan yake ko take. I don't even know me aka haifa. Bayan da ni aka yi komai" a hankali nace "Mommy you didn't ask. 17 8 5 1 10:32 PM Ni kuma naga ba dai dai bane in yi miki maganar sa" tace "ohh namiji ne kenan? Amma kin zauna da cikin sa ai a gaba na amma ba zaki iya yi min maganar sa ba" na so in bar maganar haka in koma quit mode dina but the new Fiyya in me wouldn't let go sai nace "Mommy ke kika gaya min da kanki cewa you don't want anything to do with the baby, kika ce kar in doshe ki da shi" tayi shiru tana kallona sai kuma a karshe tace "I was angry" na dauki spoon dina na cigaba da cin abinci na. Muna gamawa naga an fara fita da kaya, I asked abinda yasa zamu tafi da wuri and Hassan ya gaya min wai za'a biya ne ta gidan Safina Daddy da Mommy suga dakin ta sannan muyi mata sallama. Muna shiga mota Mommy tace "kema ai baki ga gidan Safina ba, kwa samu ku gaisa sosai". Tun sanda aka ambaci gidan Safina na nemi farin cikin da nake faking na rasa, it was so hard to even fake a smile. Tunanin nake kawai hanyar da zan bi in yi dodging zuwa gidan Safina amma kuma na san abu ne mai wahala hakan ta kasance. Har muka je muka yi packing a kofar gidan ban samu mafita ba and on impulse I used the only way da nake ganin zata fitar da ni "ban jin dadi, ku shiga ku fito kawai zan jira ku a mota" duk suka juyo suna kallona cikin mamaki har Daddy. Mommy tace "wanne irin ba kya jin dadi kuma? Ga gidan a gabanmu taku goma ya isa ya shigar da ke har ciki amma ki ce ba zaki shiga ba? Menene yake damun ki ma to?" Na nuna cikina "ina jin fitar da nayi dazu ce ta gajiyar da ni. Ji nake kamar ciwona zai bude" ta bini da kallo amma a fuskar ta naga alamar ba ta yarda da abinda nace ba, amma sai kawai ta bude kofa ta fita tana magana kasa kasa ni banji me tace ba, Mustapha da yake driving ya fita shima zai dauko kujerar Daddy a boot, a lokacin Daddy ya juyo yana kallona, na sunkuyar da kaina kasa sai yace "ki tashi ki shiga" ban ce komai ba na bude kofar na fita na tsaya ina kallon gidan. Ba gidan da na sani a matsayin na Muhammad bane ba, and hakan ya saka naji dan dama dama a zuciya ta. My heart can't take Safina da Muhammad living a gidan da nayi planning zamu yi rayuwa da Muhammad. But this one too is beautiful in dai zan ajiye kishin da yake zuciya ta. I realized akwai parts biyu a gidan, maybe daya nasa ne daya na ta, sai kuma wasu dakuna da nake tunanin na bakin sa ne daga gefe. Ta fito da gudunta, daga dukkan alamu ta san da zuwan mu, taje ta É dukkan alamu ta sai ua zuwan mu, taje ta rungume Mommy sai kuma ta fara sharar kwalla. Nan da nan hankalin Mommy ya tashi ta fara tambayar ta in akwai matsala amma sai tace mata kawai tayi missing dinta ne. Muka shiga ciki muka zazzauna, su Hassan suna ta zagaya gidan wai wancan xuwan nasu basu samu damar zagayawa ° ba amma ni sai na zauna akan kujera na fara daddanna wayata naki ma dago kaina ballantana in ga abinda zai hana ni bacci. I was relieved sanda naji tana gaya wa Daddy cewa Muhammad baya gida, "yaje gidan su, bai san zaku zo ba, na manta ban gaya masa ba" and I sensed she was lying. Ta nemi muje dining mu ci abinci, Mommy tace "ai na gaya miki dama kar kiyi mana abinci ba zama zamuyi ba, ganin ki kawai zamuyi mu wuce, sai kuma Allah ya dawo da mu gari. Amma bana jin zamu dade bamu dawo ba ai tunda ga bikin Safiyya zamu fara planning sannan kuma ga wannan aikin da ta baro mana" na dago kai ina tunanin wanne aiki ne na baro din, sai naji ta fara bata labarin maganar da nay dazu ta taking over all that is mine. Sun jima suna hirar su, Daddy da Mustapha suna dan jefa albarkacin bakin su, daga baya kuma sai Daddy yayi mata fadan da bai samu damar yi mata ba na yin biyayya ga aure, hakuri da sauran su, sai kuma yayi mana nasihar mu hada kan mu muyi zumunci da junan mu. Ni dai ban ce komai ba har aka gama. Har mun tashi zamu tafi sai Safina ta rike hannuna "20 mana Safiyya, akwai magana fa" Mommy tayi murmushi fuskarta tana nuna jin dadin ta amma sai tayi fada "wacce magana ce ba zaku yi a waya ba? To kuyi sauri dai dan ba jiran ku zamuyi ba". Suka fita suka bar mu mu biyu. 28 5 10:32 PM Na karbe hannuna daga rikon da Safina tayi masa na rungume su a kirjina ina kallon ta cikin ido. Nasan maganar and I was ready for her. Suna fita fake murmushin fuskarta ya bace tace "Mommy ta gaya mun jiya mijina yaje gida, ta gaya min yace wai na bashi sako ya kawo miki, Me yace miki?" Saura kadan maganar ta ta bani dariya amma sai nayi murmushi nace "do you really want to know?" Bata amsa ba instead sai tace "ina fatan dai baki manta ba cewa ke matar aure ce shi kuma mijina ne. If you continue seeing him I will have to tell our parents. So this is a warning. Ki fita harkar mijina Safiyya, idan ba haka ba....." Na katse ta "idan ba haka ba zaki gaya wa Mommy da Daddy, gasu can a waje, go and tell them please" muka yi shiru muna kallon juna, sai kuma naji bai kamata in bar maganar haka ba, not the new me, na cigaba "You first asked me me yace min, na tambaye ki if you really want to know amma baki bani amsa ba to bari in amsa miki nevertheless. Yaje ya sake jaddada min how much he loves me and how much he hates you. Ya kuma gaya min cewa he hates you saboda cin amana ta da kika yi.... .." Ta fara girgiza kanta, fuskarta tana nuna tsananin bacin rai '"ban ci amanar ki ba, ban san cewa saurayin ki bane ba" nace "explain that to him, not to me because I don't believe you..... ." Ta katse ni "| don't care what you believe Fiyya. I just want you out of our lives. Ki fita daga rayuwar mijina shine kawai abinda nake bukata" ta fada tana nuna hotonsa da yake makale a bangon falon, Na daga kai ina kallon hoton, ina jin bugun zuciya ta yana tsayawa a guri daya saboda kyawun da yayi min, nace "mijinki.... Safina let me give you the first and the final warning. Na daga miki kafa ne a cikin maganar nan ba wai dan ke ba sai dan shi da kuma dan ni kaina, bana son mu kasance masu sabon Allah har Allah yayi fushi da mu. Wannan shine dalilin da ya saka zan ja baya daga gare shi ba wai dan kina matsayin matarsa ba" na kara taku daya na tsaya daf da ita nace "but don't push it. Don't force my hands. In kika sake gangancin tsayawa a gabana kina yi min irin wadannan maganganun banzan zaki gane really wacece ni. Kinga wannan mijin naki?" Na fada ina nuna hoton nasa, sannan na nuna mata tafin hannu na "a tafin hannuna yake. Duk abinda nace masa yayi to tabbas zaiyi shi. Idan da ina bukatar ki koma gidan ku da zama ba ma sai na bude bakina nayi magana ba, I just have to make a sign with my hands and boom!!!! Zaki ganki a gidan babana a dakin Mommy a matsayin bazawara, ko kuma ki ganki a katsina inda yafi dacewa da ke. In baki yarda ba ki gwada ki gani. Nonsense" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Thirty Five: Petty Yar uwa kinsan illar dake tareda infection kuwa,to bari kiji kadan daga cikin illar da infection yake da ita, kinsan cewa infection yana hana haihuwa,yana hana ma'aurata jindadin mu amala,yanasa warin gaba kowane irin tirare kika sa bazai hana wannan warin fita daga jikin kiba fitar farun ruwa kaikayin gaba tusar gaba duk suna daga cikin illar da infection yakewa Ifyr ki. Ina masu fama da ulcer, Asthma,sickle, ina matar dake fama da fibriod, matsalar rashin haihuwa ko bushewar jiki da fata haddake mai son hils da breas ina uwar gida maison faranta ran oga a othe room kema ba abarkiba jawarawa da yanmata ku garzayo kuma ku kwada ku gani munada feminine wash,garlic oil da dai sauransu munada VIP chair akwai blood circulatory machine ga kuma data1g250 cikin sauki da rankwame da rahusa kedai kira number nan domin karin bayani 07035275119, 08038098317 k kiyi joining group dinmu dan gani da ido09 si kunzo ngdhttps://chat.whatsapp.com/ LqcXIrhogcQC1iLdGGNJcZ hitps:// chat.whatsapp.com/ I watched as the hurt on her face turned to rage, na juya zan fita ta kara kamo hannu na ta rike, da alama maganar ba ta ishe ta ba tace "gori? Gorin uba kike yi kin Fiyya. Do you really want to play the gori game? Ko kin dauka ban sani ba? Na san komai fa" na juyo ina kallon ta nace "Kamar yadda nima na san komai. Yes, let play the gori game please. Nayi throwing first card ina jiran naki. Menene abinda zaki goranta kin akai?" Tayi shiru yana girgiza kai, obviously trying to compose herself tace "ba yanzu ba Safiyya, time will come amma ba yanzu. Zan goranta miki ne kamar yadda kika yi min amma ba samda muke mu biyu ba, sai lokacin da yake tare da mu, I want to see the look on his face sanda zai san wacece ke, I want to see the look on your face sanda zai kalle ki idonsa cike da tsanar ki. But for now ina kara tuna miki cewa ni matarsa ce, shi mijina ne, and that's a relationship that you guys will never have. We live in the same house, sleep in the same room, share the same bed..... Na dan yi kar karamar dariya, trying so hard not to show her kishin da yake kona zuciya ta, not to let her know my weakness nace "still with the threats. Zaki sha mamaki kuwa a ranar da kika gaya masa din. A lokacin da kika gaya masa a lokacin ne zaki fahimci dalilin da yasa ban gaya masa ba. A lokacin ne kuma zaki fahimci the depth of his love for me. And maganar gida da daki da gado, ke karyar ki ai arniya ce bata sallah saboda ganin da nayi wa Muhammad jiya, da ganin da nake yi miki yanzu, plus maganganun da suke fitowa da ga bakin ki masu tabbatar da how desperate you are sun tabbatar min da cewa baku taba hada daki ba ballantana gado. Maybe only in your dreams" na karasa ina flashing mata hakorana in an ear to ear smile. Ta kara kufula, a lokacin nasan zata iya bada komai nata dan ta samu damar dukana but she couldn't. Tace "haka kika ce? Haka kike tunani? To ni kuma zan nuna miki karya kike yi wallahi. Ki bani wata biyu zuwa uku zan je har gida in nuna miki result din kwanan da muke akan gado daya, a lokacin zaki tabbatar da karya yake miki yana kuma miki wasa da hankali, sannan,….. Mustapha ya bude kofar falon ya shigo, daga alamu aiko shi aka yi ya kira ni, sai kuma ya tsaya yana kallon mu "me yake faruwa?" Ya fada yana kallon hannuna da ta rike gam, ta saki hannun ta ja baya, ya sake tambaya cikin fada "me yake faruwa nace, are you guys fighting?" Na watsa masa mugun kallo sannan nazo na wuce shi da sauri half expecting him to drag me back, half thinking cewa we are back to when we are younger, when they will team against me. Amma kuma sai na tuna cewa da da yanzu ba daya bane ba, abubuwan da suka faru a da ba zasu taba faruwa a yanzu ba. WhatsApp.com GHT team one marketing 33 WhatsApp Group Invite 18 11 2 8:25 PM Da sauri na bude kofar motar na shiga tare da rufe kofar da karfin da banyi niyya ba. Mommy ta juyo tana kallona "lafiyar ki?" Ban ce mata komai ba sai na kwantar da kaina a kofar motar na rufe idona, ta fahimci ba zanyi magana ba, ta san kuma idan ta cigaba da magana zan saka hannayena in toshe kunnuwana da su, tayi karamin tsaki "Allah ya shirya". Mustapha ya fito shima da sauri ya shiga motar yayi driving muka tafi. Har muka tsaya a airport din ban bude idona ba, ina ta yaki da tunani na trying so hard to stop picturing Safina and Muhammad akan gado daya, Sai dai ashe wan bacin ran yana can yana jirana a airport dan ina bude idona muka hada ido da Mukhtar a tsaye a kusa da Uncle Ahmad. Uncle Ahmad fuskarsa cike da fara'a shi kuma Mukhtar tasa kamar an aiko masa da mutuwa, Nayi ajjiyar zuciya "God, give me patience" dan yanzu ba strength nake bukata ba patience nake so to limit and contain my strength, in ba haka ba zan hada Mukhtar din da Uncle Ahmad din da koma wanene zai tare da ni da wata magana in dura musu yar garin su Safina, Sai dai kafin in bude kofa in fito daga Mukhtar din har uncle Ahmad din sun taho inda nake, maimakon su fara zuwa gurin Daddy su taimaka masa ya fito daga cikin motar, Nayi sauri na karasa fitowa kafin daya daga cikn6su yayi magana na bar gurin na koma kofar da Daddy yake kokarin budewa na bude masa sannan na taimaka masa ya dafa ni ya fito daga cikin motar, a lokacin Mustapha ya zagayo da kujerar Daddy a hannun sa ya bude ta sannan muka zaunar da shi a kai. Zuwa lokacin twins suma sun karaso gurin, su suka fara gaisar da uncle Ahmad ya amsa musu kamar baya so sannan ya karaso ya gaishe da Daddy, Mukhtar ma yazo ya gaishe shi, Na dauke kaina pretending as if bana ganin kalion da yake yi min, nima na gaishe da uncle Ahmad sai na koma na jingina da jikin mota ina jiran su gama gaishe gaishen su mu shiga ciki. Mukhtar ya matso kusa da ni "hey, babu gaisuwa?" Nayi masa kallo daya na dauke kai nace "good afternoon" ya jingina da motar shima a kusa da ni yace "fushi fa nake yi, ko baki ga fuska ta ba? Nace '"'hima haka, ko baka ga tawa ba?" Yace ('"na gani mana. Fuskar ki ita ce abinda /nake kallo tun da kuka shigo gurin nan, and kinyi kyau sosai. I noticed some changes daga shekaran jiya zuwa yau. You look different and sound different" naga jama"ar mu sun fara tafiya na bi bayan su da sauri, glad to cut off the conversation, amma ina yin taku biyu na jishi a gefena. "Ya Rabbi, give me patience" na sake yin addu'a a zuciya ta. Ya cigaba da magana "'baki tambaye ni fushin me nake yi ba" ban kalle shi ba nace "do I have anything to do with it?" Yace "of course, yanzu kaf duniya akwai wanda yake da things to do with me kamar ki? Duk, abinda ya shafe ki ya shafe ni kuma duk abinda ya shafe ki ya shafe ni, We are bounded together" ban ce komai ba na bi bayan Mommy zuwa lounge din da zamu jira lokaci ya karasa, Mukhtar ya shigo after me, ina zama ya zauna a kujerar kusa dani. Na dauko Wayata daga cikin jaka na fara danne dannen iska, ya saka hannu ya zare wayar daga hannu na yana kallon ta yace "so your phone is with you amma in na Kira ki bana samu. Why?" Na daga kafada "it was switched off, sai dazu na kunna" yace "liar. Jiya ta shiga ai baki dauka ba dana sake kira dai naji a kashe" nayi ajjiyar zuciya "na kuna ta briefly, ba charge kuma sai ta mutu, ban sake kumnawa ba sai yanzu" ya cigaba da juya wayar a hannunsa sannan yace "still lying. Ba kya son magana da nine. Just say it with your full chest shikenan. When I accept to marry you I know fully well what 1 am getting myself into." Ya miko min wayar yana yi min murmushi "and 1 am ready for it all. You will fall in love with me Safiyya I promise you that. One day zaki yi mamakin me yasa tun farko baki so ni ba. Because I am going to treat you like a queen, I have so many things da nayi mana planning for our lives together. And I cannot wait long kafin in cika wadannan burikan nawa a kanki, 17 16 8:25 PM Wannan yasa na yanke shawara, na gaya wa Abba and I am sure maganar da suke yi da Daddy kenan" na dago kai na kalli inda Daddy yake zaune, naga uncle Ahmad a zaune a kusa da shi suna magana, daga alama magana mai muhimmanci suke yi. And at the other side Mommy da Mustapha suna zaune looking back and forth between us and su Daddy. Na yi ajjiyar zuciya. This family of mine is full of drama. Mukhtar a kusa da ni yayi dariya kasa kasa, amma duk mutanen gurin sun ji shi dan gabakidaya sai suka juyo suna kallon mu, sai kuma yayi sauri ya rufe bakinsa da hannunsa tare da kifa fuskarsa akan kafada ta, nayi saurin matsawa daga kusa da shi ina kallon Daddy da shima yake bina da kallo sai kuma naga ya juya sun cigaba da maganganun su da uncle Ahmad. Mustapha ya mike ya bar gurin da sauri, Mommy tayi tsaki, na tabbata zuciyarta a makogwaronta take a lokacin and I pity wanda zai taba ta a lokacin. Kamar abin baki sai ga innocent twins sun shigo gurin da ledoji a hannayensu, daga dukkan alama wani abun suka siyo a waje, ai kuwa suna shigowa Mommy tayi kan su da fada "daga gidan uwar wa kuke? Kowa yana nan a zaune ku kun kama hanya kun fita? Uban me kuka siyo?" Suka tsaya kawai suna kallon ta sun kasa neman uzurin kare kan su. Mukhtar ya gyara zaman sa ya juyo yana facing dina, stylishly covering the distance dana saka a tsakanin mu. Ya ce "na gaya wa Abba ya yi wa Daddy maganar ina son ayi bikin mu in the next two weeks" na juyo da sauri ina kallon sa and he winked at me, nayi saurin dauke kaina daga kansa ina girgiza kai ne "it is not possible kai ma ka sani. Bani da lafiya, Daddy yace sai na warke tukunna" yace "and who says ba zaki iya warkewa a gidan ki ba? I need to take care of you inyi jinyarki ki warke a hannuna" ya fada yana kama hannuna, nayi saurin karbe hannuna ina yarfarwa a gefe tare da rarraba ido kamar marar gaskiya "ka bari, ka daina haka dan Allah yaya Mukhtar. Su Daddy fa suna gurin nan" ya sake yin dariya "SO nake Daddy ya yarda da maganar da Abba yake gaya masa ai. I need to be with you" ya fada almost in my ears. Na mike tsaye da sauri na rataya jakata nayi hanyar fita, ya mike shima ya wuce ni ya tsaya a bakin kofa yayi folding hannayensa, completely blocking my way, still da murmushi a fuskarsa, na bata rai nace "ka bani guri in wuce" yace "sai kince kin amince da abinda nace, dan yanzu in na barki kuka tafi ba waya ta zaki dauka ba kuma ba gain ki zanyi ba. So l need to know amsa ta yanzu even if I have to kiss you here" na juya na koma na zauna, ignoring zuciya ta da take gaya min in wanke fuskarsa da mari. Ina zama shima ya zauna a kusa da ni. Na kalli Daddy naga shima ni yake kallo, his face looked worried. Mukhtar yace '"'believe me idan aka yi bikin ke kanki zaki fi jin dadi, zaki samu ki huta sosai, ki samu nutsuwa ta jiki da ta zuciya, away from all this ... ...…..hayaniya" ya fadi hayaniyar yana waving at side din da Mommy har lokacin take yi wa twins fada. Na juya ina kallon sa raina a matukar bace "don't talk like that about her" ya daga hannu '"shikenan, na daina. Yar gidan Mommy" Uncle Ahmad ne ya dan gada murya ya kira sunana "Safiyya, come here my dear" na tashi na je inda yake zan durkusa sai ya nuna kujerar kusa dashi "seat" na zauna ina kallon sa and I noticed that 1 have never seen him this happy, shi mutum ne marar fara'a wanda tun ina karama nake tsoransa, fadan sa ba irin na Mommy bane ba, Mommy will bark and bark but she will never bite, fadan ta ya kai har bamu da mu ba in tana yi, like I can literally fall asleep a lokacin da take yi min fada. But shi ko kallon ka yayi you will feel your insides shaking. Amma lokacin he was smiling from ear to ear for me. Ya sunkuyar da kaina kasa ina kallon yatsun hannu na, I was ready for his fada, na dauka zai sauke min balai ne idan Daddy ya gaya masa abinda nace, and I already made plans for that. But he was smiling. And it threw me off balance. 22 12 8:25 PM Yace "yaya ya gaya min sakon ki, and I am very happy with your decision. I would have said nan da next two weeks everything will be ready for you but your husband is pressuring me cewa nan da two weeks yake so ayi bikin su, and I cannot do two things at the same time" nayi shiru ban ce komai ba sai ya cigaba "mun riga munyi magana da yaya mun kuma yanke hukunci, amma ke ya kike gani? I want to know your opinion" na dago kai na kalli Daddy, bana son in fadi abinda ba shine abinda ya yanke din ba amma sai naga ya gyada min kai, I took it to mean in fadi abinda yake raina, Nace "if you can make the arrangements within two weeks din shikenan sai ayi wannan din first, Bikin sai a kara lokaci" ya kalli Mukhtar da yake zaune a inda na taso yana kallon mu, maybe trying to guess abinda muke cewa, sai yace "hmmm, your husband isn't going to like that. Amma sai dai yayi hakuri. Kamar yaushe kenan kike so a saka bikin?" Na ji ina feeling very uncomfortable. Ba zan iya maganar bikina da iyaye na ba. Sai na juya na kalli Mommy nace "Mommy uncle Ahmad yana magana" sai na dawo da idona O kansa nace "Mommy will take care of that. Maganar ta ce ba tawa ba" and I instantly saw bacin rai a idon uncle Ahmad. Amma kuma na lura hakan yayi wa Daddy dadi. Ta taho ta zauna a kusa da Daddy tana tambayar sa menene, Daddy ya fara yi mata bayani, nan da nan tace "at least wata uku za'a saka" uncle Ahmad yace "wata what?" Ni dai na mike na bar su da wannan. Mercifully tun kafin in zauna aka shigo aka gaya mana mu fito, Ban jira komai ba nay hanyar waje twins suka bi bayana suka tsaya a sides dina muna tafiya tare, Hassan yace "it was too hot in there, and all the acs are working" Hussain yace "zafinai bana gari bane ba, Mommy tana ciki, uncle Ahmad yana ciki, how can it not be hot?" Suka yi dariya a tare, na saka both hannayena da daki jeyoyinsu a tare, Suka sake yin dariya sannan Hussain ya miko min ledar hannunsa yace "ga ice cream ki sha ki sanyaya zuciyar kj" na karba ina jin dadi a raina nace "thank you, I really need this". Sai bayan da na shiga na zauna na bude ice cream dina zan fara sha sannan na tuna ko kallon inda Mukhtar yake banyi ba ballantana muyi sallama, and I didn't care. Mommy ta shigo ta zauna a kusa da ni ta cigaba da mita "wai sati biyu, kiji fa wani rainin hankali. Ko yar tsana ai ba za'a yi bikinta a cikin sati biyu ba. Da akwai kayayyakin da ba zamu same su a Nigeria ba sai munyi order, akwai mutane da zamu gaiyata da suke bukatar noticed tunda wasu ba'a kasar nan suke ba, ga shi ba'a jima da bikin Safina ba mu kan mu bamu huta ba, gashi...... ." Na kwantar da kaina ina kallon ta nace "Mommy relax. You already had your dream wedding a bikin Safina, Ni bana bukatar taro a nawa, there is no going to be a dinner or any of those bridal things, Sai dai in ku iyaye zaku yi naku, Amma ni babu abinda zanyi" ta ce "kina nufin kin amince da sati biyu kenan?" Na girgiza kaina "no, Ba dai sati biyu ba, Ina da abubuwa da yawa a gaba na. Ina bukatar in huta kuma, Duk watannin da kike ganin sunyj" ta tabe baki "na fahimci manufar Ahmad ai. Zancen karbar dukiyar da kika yi shine ya jawo wannan sati biyun, kinga yana nufin ko kin karba zaki koma hannunsa ne daga ke har abinda kike da shi. Ni na riga na gane duk tactics dinsa, watarana kema zaki gane. Fata na dai kawai ki gane da wuri tun kafin ya zama late. Dan daga kun fara haihuwa magana ta kare. And wannan marar kunyar dan nasa......... Na tabbatar da Adam lafiyar sa kalau, da ace da ne da sai ya wanka masa mari yayi resetting brain din dan iska... Ta cigaba da surutan ta ni kuma na kwanta na rufe ido na ina jujjuya maganar ta da ta dauki hankali na. "Zancen karbar dukiyar da kika yi shine ya jawo wannan sati biyun, kinga yana nufin ko kin karba zaki koma hannunsa ne daga ke har abinda kike da shi" shin wannan shi ya saka bai nuna damuwa ba kamar yadda nayi tsammani ko kuma da gaske bai damu ba din? In dai kuwa har abinda ta fada shine plan din sa then he is really in for a surprise, They all are really in for a surprise, Him ©️ 22 10 2 8:25 PM Sanda ya bar gidan su Safiyya his mind was running in all different directions. Ya kasa tsayar da tunanin sa guri daya. Ya kasa fahimtar me ya faru. Ya kasa fahimtar me ya far ballantana yayi preparing for menene zai faru next. He just saw Safiyya and they talked, more calmly now then last haduwar su. But still the calmness was from Safiyya not from him. Ta hana shi cigaba da magana da Daddy, and obviously that means bata son Daddy ya sam tsakanin su and his mind is telling him cewa dalilin ta is deeper than him being her step sister's husband or she being married. Akwai wani dalili mai karfi aside those. And yana so ya san menene dalilin. And then she told him she loves him. Kalmomin da suka ratsa fata, tsoka, katsi da bargon sa suka shiga jinin dake gudana a jijiyoyin jikinsa sannan suka sauka a zuciyarsa, Casually ta fade su, Maybe she didn't even think much before saying them but sun yi matukar tasiri a gun shi. He needed those confirmatory words. Tunda abin ya faru lalube kawai yake yi cikin duhu, thinking, analyzing and making assumptions amma yanzu ya samu tabbas. She loves him Sai dai kuma sanin haka ya kara jefa shi cikin rudani, menene ya faru da zai saka ta ki auren sa duk da son da take masa ta auri wanda da bakinta ta fada cewa bata so? Menene ya faru da yayi stripping dinta of all that makes her? He just kept driving and passing unguwanni without knowing exactly ina zai je, idan yana cikin irin wanna yanayin yana son yin driving especially a outskirts of town inda babu traffic, it clears his mind and increases the dept of his thoughts. Ya samu amsoshi da yawa a binciken sa amma kuma a karshe ya hadu da dead end, Safiyya ta toshe duk kofofin binciken 0? sa, She said she wants him to accept and face his fate, Amma kuma sai ta nuna kishin ta a fili da ya ambaci sunan Safina a matsayin fate din nasa, It is obvious cewa auren sa da Safina yana damunta sosai. Shima kuma yana damunsa sosai, sai dai his hands a tied a yanzu, In dai har ba ya samo wata hujja kwakwkwara ba bashi da damar rabuwa da Safina dan hakan zai shafi alakar sa da mahaifan sa sosai. Yana bukatar wani abu da zai presenting to them a matsayin dalilin da yasa ba zai iya zama da Safina a matsayin matar sa ba. Kiraye kirayen sallah ne ya dawo dashi hankalin sa ya juya kan motar zuwa hanyar gida. Sai da yayi packing sannan ya ga dauko wayarsa, sai a lokacin yaga missed calls din Safina guda 5. Yayi tsaki, shi ya ma manta da ita a gidan Mommy. Yanzu kuma Mama zata ce sai yaje ya dauko ta. Watakila ma already har ta kira Mama tace mata ta neman sa bata same shi ba. Ya jira sai da yaga Abba da Haidar sun fito zasu tafi masallaci sannan ya bude motar ya fita ya bisu suka je suka yi sallah tare suka koma gida, Yana zama a falo Haidar ya fara tsokanar sa "anya kuwa wannan amaryar ta iya girki? Kullum sai kazo ka ci mana abincin gidan mu?" Yaji ranshi ya baci duk kuwa da cewa ba abin bacin rai Haidar din ya fada ba, Mama ta karaso inda suke da charbi a hannun ta tana cewa "muryar wa nake ji ne anan, Gidado no banga amfanin wayarka ba wallahi. Gabakidaya yanzu ka chanja hali sai a kiraka sau goma ba zaka amsa ba, idan kuma emergency ne ya faru fa? Mutum ya ajiye iyali amma baya daukan waya?" Bai vi kokarin kare kansa ba sai ya gaishe ta, ta amsa sannan tace "dazu Safina ta kira ni tana tambayar ko kana nan nace mata ba ka nan, ta kira wayarka baka dauka ba ni ma na kira ka baka dauka ba" yaji haushin Safina ya karu a zuciyarsa, yace "'ai ta san ina tare da mutane, niyya ta in zan tafi gida in biya in dauke ta mu tafi" Mama ta bishi da kallo tana lura da yadda ransa yake a bace. Sai tayi shiru bata sake cewa komai ba. Abba yace "ka bata waccan motar ta ka da baka hawa mana, ka huta da kaita unguwa da kuma daukota" "to"' kawai Muhammad yace ya sake yin shiru zuciyar sa tana burning a kirjinsa, so yake kawai ya samu abinda zai daka yaji dadi. Mama ta sake cewa "tun dazu ta kira ni wallahi, da yake tana da kunya shi yasa bata gaya min jiransa take yaje ya dauke ta ba ta dai ce min ta kira number din sa bata same shi ba, 19 12 2 8:25 PM Kuma tunda bata saba da mutanen gidan ba kamar she sounds uncomfortable". Muhammad ya mike da sauri ya dauki key din motar sa yayi hanyar waje, Mama tace "ka fasa cin abincin ne? All through yau fa ina jin baka ci abinci ga idanunka nan duk sun fada" ya juyo "na fasa cin abincin tafiya zanyi. It seems like you people don't want to see me here anymore. Gwara in tafi in bar muku gidan ku". Gabakidaya suka saki baki suna kallon shi, bai taba yiwa Mama magana irin haka ba. Sai kuma yayi realizing da wa yake magana yaji wani iri a zuciyarsa. Ya dawo a hankali ya koma ya zauna tare da dafe kansa. Abba yace "Gidado lafiya kake kuwa? Menene ya hau kanka yau?" Mama kuma tace "Muhammad waye a bata maka rai haka?" "Am sorry" ya fada a hankali sai kuma ya sake tashi ya tafi dinning table ya fara zuba abinci not knowing me yake zubawa ma. Mama ta biyo shi ta karba tana zuba masa sai ya koma ya zauna, ta ajiye masa plate din a gabansa sannan tace "me yake damun ka Muhammad? Talk to me" ya fara jujjuya spoon din hannunsa yana kallon ta, shi ya san the moment da ya ambaci sunan Safiyya gabaki daya sai rayukan su sun kara baci, maybe ma cewa zata yi akai shi gidan malamin ruaya ayi masa. Ta sake tambaya "Safina ce? Are You not happy with her?" Ya sake yin shiru yana tunanin iyakacin abinda ya kamata ya gaya mata, at the end yace "I just don't like her" tayi ajjiyar zuciya "Muhammad... ..... Don't you think it is a little bit too late for that? Tun kafin a fara maganar nan sai da aka turo maka pictures dinta ka ganta, and then you went to gidan iyayen ta ka sake ganin ta face to face sannan kace ka amince sannan aka fara maganar nan. Abban ka yace har a day to daurin aure sai da ya tambaye ka idan ka amince ace masa ka amince. Sai yanzu bayan an daura har ta tare sai kace bata yi maka ba kuma? Will it be fair to her and to her parents idan muka ce an fasa kuma yanzu? Ko wata behavior tayi maka yanzu da ta saka kaji haka?" Bai bata amsa ba Abba da Haidar suka zo gurin, Abba yana kallon sa yace "kaga dan lelen mamansa, ta zauna tana ta lallaba shi kamar wani jariri. Ko Mufida ba'a lallabawa haka" Haidar yace "'ballantana ni" daga Muhammad har Mama babu wanda yayi magana, Muhammad ya fara cin abincin da ta zuba masa yana hadiye wa kamar mai shan magani ita kuma tayi tagumi tana kallon sa, babban tashin hankalin ta a duniya shine taga yayanta cikin damuwa, babban burinta shine yayanta suyi living a happy and fulfilling life. And she is determined to get that for them in all the possible halal ways.…. Suka gama in abincin sannan suka dawo falo suka zauna, ganin basu sake yi masa maganar ya tafi ba sai yayi kwanciyar sa akan kujera yana jin dadin presence din iyayen sa a yare da shi da kuma muryoyin su suna tattaunawa akan random issues, har akayi sallar isha, ganin bashi da niyyar tashi kuma bata son matsa masa sai Mama tace "Haidar tashi ka dauki mota kaje gidan Mommy ta dauko Safina ka taho da ita nan gidan"., Muhammad yana jin ta fadi haka sai ya gyara kwanciyar sa aka kujera ya chanza tasha a tv, amma maimakon yayi kallon sai ya mayar da idonsa ya rufe, Yana nan a kwance har yaji tsayuwar motar Haidar ya dawo, yaji shigowar sa sannan yaji sallamar Safina, ta gaishe da Abba sannan ta gaishe da Mama, Yaji Abba yayi musu sallama ya shiga ciki, sai kuma yaji Mama tace "sannun ki, kin sha kuma yaji Mama tace "sannun ki, kin sha zama" Safina tace "babu komai Mama" and he noticed muryarta tayi kasa sosai. Mama ta fara kokarin tashin sa "'Muhammad Gidado" ta fada tana shafa kafarsa, sai kuma ta danyi dariya nervously "yayi bacci. Abin mamaki. Muhammad baya bacci akan kujera. In dai kinga yayi bacci to sai yayi wanka ya chanja kaya ya kwanta akan gado, ba'a ko ina yake yin bacci ba. Kinga mai bacci nan a ko'ina. Shi wannan ko akan siminti ne kwanta yayi bacci" ta fada tana nuna Haidar, Haidar yace "haba Mama kar ki tona min asiri mana" Mama ta sake taba Muhammad "Muhammad ka tashi fa, dare yana kara yi" Safina tace "maybe he is exhausted" Mama tace "ai kuwa dolr ya tashi, wannan kwanciyar ai sai jikinsa yayi ciwo. Muhammad!" Ta fada da dan karfi tare da taba fuskarsa. 24 6 4 8:25 PM Yana bude ido suka hada ido da Safina, ya dauke idonsa daga nata sannan ya tashi zaune, Mama tace "ka tashi ka bar yarinya tana ta hamma ta gaji" ya mike tsaye sannan involuntarily yayi mika. Haidar yayi dariya "wai! Wa yaga zangina ba da sunan wani ba" Mama tace "tubarkallah" Muhammad ya juyo yana kallon sa ya hade rai yace "yaushe na fara wasa da kai?" Sai kuma yayi wa Mama sallama sannan ya dauki key din motar sa yayi waje ba tare da ya kalli inda Safina take ba. Yaje ya kunna motar ya kunna kida sannan yayi zamansa a ciki, yana kallon ta ta fito ita kadai ta taho zata bude kofar motar sai yayi locking sannan ya dauke kansa gefe kamar bai san tana gurin ba. Tayi knocking window din motar sai ya kara volume din kidan da ya saka. Ta ja gefe daya ta tsaya kusan five minutes sannan ta zagayo side din da yake ta sake knocking, ba tare da ya kalle ta ba ya bude lock din sannan ya nuna mata kofar da hannun sa, sai da ta sake zagayawa sannan ta bude ta shiga. Tana shiga kafin ta gama rufe wa ya ja motar, tayi sauri ta rufe kofar tana kallon sa da mamaki, sai a lokacin ya lura da cewa kuka take yi, hawaye ne shabe shabe a fuskarta, Suna daukan hanya tace "ka kaini gidan mu" bai kalle ta ba yace "sai dai in ajiye ki anan ki samu motar da zata kaiki tasha ki tafi Katsina" tace "ai ba'a Katsina ka dauko ni ba" ya juya yana kallon ta yace "actually ba'a ko ina na dauko ki ba, Ke kika zo da kafafuwan ki. In zaki tafi ma da kafafuwan ki zaki tafi" tayi shiru bata sake cewa komai ba suka cigaba da tafiya, sai kuma yace "nan gurin yayi ko in kara gaba? A ina ne inda zaki fi samun abin hawa? Ko in ajiye ki zaki karasa da kafarki" ta goge hawayen fuskarta da yaki tsayawa tace "why do you have to this mean? Da me kake so inji Muhammad? Kana so in mutu ne wai?" Yace "you bought it da kudin ki. Da kudin ki kika saka kika sayi duk abinda nake yi miki, and I will keep delivering what you bought har sai ke da kanki kince ya ishe ki haka kin koma gidan ku" Ta cigaba da kukan ta "Mommy tace min kaje gidan mu, and you said wai na baka sako ka bawa Fiyya. Ashe dama wajanta zaka je kace wani business issues ne? Muhammad matar aure ce fa. Ba ka tsoron abinda Allah zaiyi maka akan hakan? Baka tsoron abinda Allah zai yi maka akan abinda kake yi min?" Yace "point of correction, Dazu naje gidan su Piya ba gidan ku ba, Why are you associating yourself with them bayan you didn't consider them important enough kiyi mentioning dinsu to wanda zaki aura? Ke fa kika ce min ke yar Katsina ce. Ta ya akayi kuma gidan da yake Abuja ya zama gidan ku?" Bata amsa ba, ya sake cewa '"kina son jin maganar da muka yi ne?"' Ta dauke kanta gefe "kaji tsoron Allah. Allah yana kallon ka, and kayi tunanin abinda Mama da Abba zasu ce idan suka sanj" ya taka burki da saurin da sai da ta kusa buga kanta a jikin dashboard, ta juya tana ( kallon sa ta ga ya hade rai kamar bai san kalmar imani ba yace "this will be the first and the last time da zaki yi threatening dina, and dazu will be the first and the last time da zaki kai magana ta gurin iyaye na. I don't joke with my parents and I swear you will regret knowing me idan kika yi trying hada ni da su". Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Thirty Six: The Boss Lady (©️ 243 X Wani tsoron sa taji ya kamata, ta dauke idlonta daga cikin nasa ta sauke su a kasa, ya maimaita cikin tsawa "do you understand?" Ta gyada kai da sauri tana jin wasu sabbin hawaye suna biyo cheeks dinta. Ya ja motar suka cigaba da tafiya yana jin ransa yana kara baci, yarinyar nan ba karamin raina masa hankali ma tayi ba wallahi, wai har shi zata yi threatening cewa zata gaya wa iyayensa maganar Piva? Amma kuma a kasan zuciyar sa ya san toro ne ya kara masa bacin ran, he just couldn't imagine bacin ran da Mama zata shiga idan taji cewa har yanzu bai rabu da Safiyya ba duk kuwa da irin rabuwar da suka yi da kuma kasancewar ta matar aure, duk kuwa da auren da suka rufe ido suka yi masa shima, Maybe ranar kwana zata yi tana kuka, And he will never let that happen ko da kuwa a mafarki ne. Ian Safina kuwa tayi gangancin faruwar hakan to tabbas sai dai taje asibiti a saka mata hakoran roba dan sal ya zubar da wadanda suke cikin bakin ta. Babu wanda ya sake cewa komai a cikin su har suka shiga gida suka yi packing. Sai kuma duk suka zauna a motar basu fita ba. Ya juya ke nan zaiyi mata bala'in ta fita ta bashi guri sai ita ma ta juyo tana kallon sa da kumburarrun idanun ta tace "Kayi hakuri Habibi, na ga ranka ya baci sosai akan maganar su Mama. I will never do abinda ba ka so. Ko da kuwa kai zaka cigaba da yi min abinda bana so ne" ya girgiza kansa cikin mamaki "you are one darm manipulative woman. Ba zakiyi abinda bana so ba kika ce. And the first thing da kika yi a rayuwar mu da ke was abinda na gaya miki point blank cewa bana so, and it turned out to be the only thing da kika iya yi, karya. You are a liar and it seems like you will always be a liar" ta saka yatsun hannunta da har lokacin suke duke da lallen bikin ta ta goge hawayen fuskarta tace "you are really hurting my heart. Allah shine shaidata. Ni banyi maka karya ba" yace "get out of my car" ta bude kofa ta saka kafafuwanta a waje zata fita sai kuma ta juyo tana kallon sa tace "wannan amsar da kake ta nema, It looks like ba ka same ta ba yau ma, And knowing kun hadu da ita tells me cewa ta toshe hanyar samun amsar ta ka kenan, Meaning she lied to you again, And here you are shouting at poor Safina cewa ba ka son karya" ta karasa fita daga motar dan kallon da yayi mata anything can happen in ta cigaba da zama kusa da shi. Amma maimakon ta rufe kofar ta tafi sai ta cigaba da magana daga waje "na san amsar, amma ba zan gaya maka ba saboda dalilai uku. Na farko saboda ina sonka bana son abinda zai bata maka rai. Na biyu saboda ka riga kayi tagging dina a matsayin makaryaciya dan haka ko na fada ma ba zaka yarda ba, gwara ka ji a wani gurin. Na uku kuma because you did not ask me nicely, try asking me nicely, watakila in gaya maka" sai kuma tayi sauri ta juya ta yi cikin gida har tana hardewa saura kadan ta fadi. A ranta tana jin dadin ko babu komai yadda zata kwana da takaici haka shima zai kwana da shi. Ya bita da kallo har ta shige ciki ta mayar da kofa ta rufe, a zuciyarsa yana mamakin audacity irin na Safina. Ya tabbatar ba dan gudun bacin ran iyayensa ba da ace zuciyar sa zai bi da either Safina ta kwana a asibiti ko kuma a gidan babanta, or better put, gidan baban Safiyya, Ya jima a zaune a motar kafin ya tashi shima ya shiga nasa part din. Kamar yadda Safina tay target, duk su biyun ba su samu nutsatstsen bacci ba. Part of him knows that gaskiya Safina ta fada cewa Safiyya tayi masa karya, amma ya rasa dalilin da yasa baya daukan karyar tata a matsayin babban laifi kamar yadda yake daukan ta Safina. Yana yi mata uzuri saboda yana son ta, yana son ta sosai. Sai ya fahimci cewa babban weakness dinsa a rayuwa shine Piya. Ya tuna sanda suke tare sau da yawa yana gaya wa kansa haka, yana gaya wa kansa cewa idan suka yi aure dole ya san yadda zai ringa tankwara ta akan abinda yake ba dai dai ba., Amma a zamanin soyayyar su duk abinda tace shikenan magana ta zauna ko da kuwa a zuciyarsa ya san ba hakan ya kamata ayi ba. Ya tuna watarana da tazo office din sa……… "Yaya Muhammad" Ya dago kai da sauri tare da sakin baki yana kallon ta, Ta sake maimaitawa "'Yaya Muhammad dina" Ya ajiye biron hannunsa yana dariya "Wonders will never end in this world, Yau kuma Yaya na koma? Ina kika bar Malam Muhammadu dan fillon and the rest of the names you used to call me" Ta zauna akan kujera tare da langwabe wuya ta turo baki. Yayi tagumi da hannu daya yana kallon ta fuskar sa da murmushi, ya lumshe idonsa yace "those lips ........ I wonder what they taste like" ta mayar da su da sauri sannan ta mike ta dauki jakarta tayi kamar zata fita, yana dariya yace "sorry fiyyan Daddy, na daina tsokanar ki, zo ki gaya min me ya faru" ta tsaya a bakin kofa, dama kuma bata yi niyyar fita ba barazana ce kawai. Sai ta juyo ta nuna shi ta ce "zan rama, Ka rubuta ka ajiye" yace "ba damuwa, Bana jin tsoro, Ina nan ina jira" ta koma ta zauna tana kallon sa tana jujjuya hannunta, yace "uhumm, ya akayi? What's up with all the lallabawa and the Yaya Muhammad" tace "dama wan labari zan baka, Kana ji ko? Uhmmm, biki ne za'a yi next weekend a gidan su Safina yace "your step sister?" Tace "yes, to za'a yi bikin half sister din ta. Shine Mommy tace mu shirya mu tafi muyi sati a can. Zasu z0 su dauke ni this weekend sai mu wuce" tayi shiru, ya gyara zamansa yana juyi akan kujera yana studying dinta, she looked disturbed, ta jima sannan ta karasa maganar a hankali '"'I don't want to go" ya ajiye pen din hannunsa yana kallon ta yace "then tell Daddy. Ki gaya masa ba kya son zuwa shikenan" ta kwabe fuska tana shirin sa kuka tace "na gaya masa ai, sai yayi min hayaniya a waya wai sai naje" yace "okay then go. Menene abin damuwa a ciki? You guys have been living together for years. Kun saba. And Daddy wants you to go da haka yana da dalilinsa. Kiyi masa biyayya mana ki je" "I don't want to go" ta sake maimaitawa. Yayi ajiyar zuciya, ya san wanna fuska, ba zata je ba. Yace '"to yanzu menene nawa a ciki? What's with the Yaya Muhammad thing" tayi murmushi tare da gyara zamanta tace "yauwa. Dazu na gayawa Daddy cewa ina da test har guda four a next week, amma sai yace karya nake yi tunda already na gaya masa bana son zuwa" yace "and he is right" tace "yes, but I want him to believe cewa da gaske nake" ya sake cewa "ni fa har yanzu ban gane role dina a wannan maganar ba" tace "so nake ka rubuta takarda, using the school's letter heading and stamp, cewa next week satin c.a ne dan haka ana bukatar kowanne dalibi ya kasance a present, wanda baya nan ba za'a yi masa make up c.a ba". Ya bude ido "Piya? What's lying and forgery, it can cost me my job" tace '"makarantar ta su waye?" Yace "ohh, kina nufin uncle Habib will take it lightly with me idan ya kama ni da wannan laifin?" Tace "it is not as if zamu kafe takardar ne a notice board, Daddy kawai zan turawa a waya ya gani shikenan" ya girgiza kansa am not going to do it Piya. Ba zamu hada baki muyiwa Daddy karya ba. In ya gane ba zai ji dadi ba kuma ba zai kuma yarda da maganar mu ba" desperately tace "please 🥺"' ya sake cewa "no. And I mean no. Magana ta kare". Ta cigaba da zama tana hararar shi shi kuma ya jawo system dinsa yana daddanna wa pretending as if bai san hararar sa take yi ba, Sun jima a haka sannan tace "dama ni damuwa ta shiga cikin bikin ne. Naga sun shirya a lot of dinners and parties, I just don't want to mingle with mazan gurin. Ka san samari in suka ga yammata sababbin fuska...... Amma tunda ba zaka yi min ba I will just have to go and mingle with them" ya danyi murmushi sannan ya dago yana kallon ta, ta dauke kai gefe alamar tayi fushi, yace "I understand what you are trying to do. You are trying to get to me and I will not let you" ya cigaba da danne dannen sa. Ta juyo tana kallon sa ta sake cewa "Please mana Yaya Muhammad, haba mana" ya sake cewa "no! We will not do it" 20 16 2 10:12 PM But five minutes later har ya gama rubuta takardar yayi printing, tana tsaye a kusa da shi fuskarta kamar gonar auduga, ya dauko biro yayi signing a inda ya kamata ayi signing a grin. Ta miko hannu zata karba "thank you, thank you so much" ya janye takardar "uhmm uhmm. I am not going to give it to you" ta bata rai sai va wuce ta zuwa dan karamin board din da yake kafe a office din nasa ya dauko pin ya makala takardar a jiki sannan ya dauki wayarta da take ajiye akan desk dinsa, fingerprint dinsa yana iya budewa kamar yadda nata yake bude wayarsa, ya bude wayar sannan ya dauki hoton takardar da take makale a jikin board din. Ya mika mata wayar, "Send the picture to him, sai kice masa a notice board aka kafe muku" ya yage takardar da ya kafe ya yayyagata ya zuba a waste bin. Ta cigaba da murna, yace "it is still a risk, idan bai zama convinced ba he can get worried and start to investigate" ya danyi murmushi kuma sannan yace "but on a positive note, in aka kamu mu I may finally get to meet Daddy. Shi yasa mana saka signature dina" ta bude ido "what??" Ya daga mata gira yana murmushin "yes! It is an invitation. And you will be the one to take the risk of sending it". But his invitation wasn't accepted. Daddy believed Piya and didn't investigate. Now here they are one year later. She married to her cousin and him married to her step sister. ** . . . . ** Ganin baccin ba zai yiwu ba and the burning in his heart yana karuwa sai ya tashi yay alwala ya kama sallah dan ya sanyaya zuciyar sa, Washegari yana tashi yayi ordering for gym equipments, sannan ya fito with the help of maigadi suka kwashe kayan da suke spare room dinsa suka saka a store sannan suka yi getting the room ready to be his private gym. And it became his solace during the evening hours and on weekends. On work days kuma ya mayar da hankali sosai akan aikinsa har sai da Abba da kansa ya yaba masa, but shi duk yanayin wadannan ne to keep his head straight and his mind occupied. Her🧕 First two weeks din mu a Kano nayi spending din sune wajan taking very good care of myself, care of my physical and mental health. Tun two days da zuwan mu gari naje asibiti na ga Dr Salma na gaya mata what have been happening so far and I also told her about the car opening scenario with Mukhtar. SHe wasn't as concerned as I thought she would be. Ta fada min cewa ina healing sosai tunda har nazo da kaina na bata labari, and she also noticed chances a confidence dina tun daga yadda nake yi mata magana. Sai ta bani antidepressants to help me control my emotions sannan kuma ta bani sharawar inyi avoiding anything that will trigger my emotions, Sai dai wannan ne kuma nake ganin kamar da wuya, Because I am surrounded bv emotional beinas, Mommv kullum cikin korafi take akan maganar biki na "wannan ai son kai ne wallahi. Kiri kiri sun nuna dan su suke so basu damu da ke ba. Shikenan dan yace ga ranar da yake so a akai mishi ke sai kawai a dauke ki kamar wata yar tsana a kaki? Shi kuma Daddy yaki cewa komai. Ni kuma ko sama da kasa zasu hade ba za'a bikin nan a kasa da wata biyu ba". And Daddy was always like "ki yi kokarin gyara tsakanin ki da Sa'adatu da yayanta. Sune family dinki a yanzu. Bana son duk wani abinda zai jawo baraka a tsakanin ku. And then in na kebe kaina to get away from them, sai tunanin Muhammad ya addabi zuciya ta, tunanin Muhammad da Safina a gida daya, daki daya kuma akan gado daya. And that thought kept my nights long. On the other hand kuma ga Mukhtar da ya addabi rayuwata, sometimes I even find myself questioning my decision to marry him, amma kuma in ba shi ba wa zan aura? Daddy has limited my options. A raina ina jinjina girman kaddarar da take tunkaro ni, Kaddarar zama da Mukhtar a gida daya a daki daya a kan gado daya, And that thought kept my days long, Daga baya dai Mommy ta gaya min sunyi reaching agreement da su uncle Ahmad akan tariya ta, sun saka six weeks from ranar da muka taho daga Kano. Daga nan kuma sai ta zama busy, ita ce Abuja ita ce Lagos ita ce Kano, ranar nan mace min tayi Maiduguri zata je. "Akwai turaruka da kayan gyaran jiki na amare da zanje in karbo miki, akwai friend dina da na saka tayi min order dinsu daga chadi, ita ta kawo wa Safina ma a lokacin bikinta" nace "Mommy ai ba sai kinje ba. She can send it to you ai" ta girgiza kai "gwara inje dan in tabbatar an hada min komai. Bana son mistake". Sai na fahimci ba wai dan ba za'a iya kawo mata sakon bane ya sa zata 5 je ba, ita kawai bata iya zama ne a guri daya. Kamar yadda muka yi da uncle Ahmad, two weeks da zuwan mu Kano suka zo gabaki dayan su. Duk wanda yake da ruwa da tsaki (stakeholders) a cikin affairs din dukiyar Ammi yazo kano a ranar. Dama tun two days to the day uncle Ahmad ya kira ni ya sake tabbatar min da zuwan nasu, muna gama waya da shi sai kuma Mukhtar ya kira ni shima ya gaya min cewa uncle Ahmad ya nemi ya shirya su taho tare "I just want to let you know ni zuwa zanyi dan in ganki, I have no business with taron da zaku y", Muna gama wayar na zauna ina murmushi ina kuma juya wayata a hannuna. People are so predictable. Ranar da zasu zo din ban tashi da wuri ba sai da nayi dogon bacci dan in samu nutsuwar da nake bukata. Ina tashi Mommy ta shigo tace Daddy yace a gaya min bakin sun fara zuwa. Na tashi navi wanka na shirya in another of my mother's attire, ba wai dan bani da wadanda suka fi su ba sai dan ina bukatar ta a tare da ni, anything that belongs to her gives me courage. Na dauko wata sarkar ta itama na saka, dan karamin 43 pendent ne with matching earrings, it is simple, classy and unique. Na saka rings guda biyu a yatsun hannuna sannan na yafa mayafi na na fito. Ina fita naga Mommy a zaune tana kallon hanyar da zan fito, muna hada ido tayi murmushi tace "you look good, sai dai baki ci abinci ba" nayi mata murmushi nima nace "| am fine Mommy, in na dawo sai in ci" dan a lokacin ji nake yi abinci ba zai iya wucewa daga makogwaro na ba, Na sauka kasa cikin tafiya ta nutsuwa ina kara tattaro courage dina sannan na bude kofar falon Daddy inda anan na san bakin zasu zauna, Ina bude kofar duk suka juyo suna kallona, naji kamar in mayar da kofar in rufe sannan in ruga da gudu in koma daki in lulluba a cikin bargo and become the little girl I once was. Sai dai na san hakan is not possible. Na san cewa wancan lokacin ya riga ya wuce ni. And then I understood gatan da Daddy yayi min da ya boye min all these maganganu ya barni nayi normal childhood dina. Bai bari na sani ba sai lokacin da yake tunanin I am old enough to handle it. That I am old enough to understand. Lokacin da na cika shekara ashirin a duniya. Few months after his diagnosis. *. *. *. *. *** 2 years ago….. Ranar birthday na ne, ranar da na cika shekaru ashirin a duniya. Daddy ya shirya min dan karamin birthday party and I was O? so happy saboda shi ba mutum bane mai irin wadannan abubuwan, abu in dai na bidi'a ne da shagali to aikin Mommy ne, But that day shi yayi min komai kuma naji dadin hakan sosai, iyakocin mu yan gidan ne kawai yan partyn nawa, sal photographers da suka zo suka yi kin pictures, suka kuma dauke ni tare da yan partyn nawa su Safina da Mustapha da Mommy da twins da kuma Daddy. Amma kuma ga mamaki na sai naga uncle Ahmad yazo shima, daga alama kuma tun daga Abuja yake, a tare da shi kuma akwai wadansu mutane su biyu. They all smiled and nodded at me amma kuma sai zuwan nasu ya saka ni na zama uncomfortable. Ina tunawa cewa sanda na yanka cake dina na gutsira naji dadin sa, the first thing that came to my mind was Muhammad, a take na yanke shawarar zan yanki cake din in yi masa preserving, in zan koma makaranta in tafi masa da shi. Bayan na gama ne Daddy yace a zo a zauna ayi min addu'a. Muka zazzauna gabaki dayan mu har bakin da ban sani ba. Uncle Ahmad yayi min addu'ar tsahon rai da rayuwa mai albarka muka shafa sai naji Daddy ya fara magana. 17 8 10:12 PM "Alhamdulillah, Allah shine abin godiya, Tun muna lissafawa Safiyya kwanaki a duniya har muka koma lissafa mata watanni sai kuma aka fara lissafin shekaru yanzu gashi har tayi ashirin. She is now a big lady" ' '"'gir'" na fada ina dariya, yayi murmushi shima yace "big girl. Ita bata son ta girma. Tafi son kullum tayi ta zama a yarinya tana ta yi mana shawaba muna lallaba ta. But it is not going to continue like that. Dole ki mike ki karbi girma ki kuma karbi nauyin da Allah ya dora miki. Nauyin da mahaifiyar ki ta dora miki" Jin ya ambaci mahaifiyata sai ya fahimci he was talking about something else, something serious. And then he said it. '"Bayan haihuwar ki, she transfered everything da take dashi to you, as a gift. Everything" nayi shiru ina kallon sa, analyzing and deciding menene everything din. Kayan dakinta? Kayan sakawarta? Maybe her car and a little change da take da shi a bank? And then one of the men da suka zo tare da uncle Ahmad said it "wannan ya hada da half of all your father's companies, a share in The Glitters Gold Company, a share in ........ ," He kept talking and talking har sai da naji kaina yana ciwo, naji my life tana turning upside down, naji bana fahimtar komai, Sai da yayi shiru sannan uncle Ahmad ya cigaba "wannan abubuwan da aka lissafa was at the moment of the transfer of ownership, bayan rasuwar ta mahaifinki yayi making some changes, an siyar da abubuwan da muke gain ba zasu yi miki amfani ba kamar motoci da sauran kananan kadarori, an kuma siyar da wadansu daga cikin kananan hannayen jarin da muke gain babu riba mai kyau ta long term a tare da su sai aka hada da cash din da yake hannu a lokacin aka kara akan wadanda muke gain sun fi long term benefits. Wadannan sun hada da kamfanonin mahaifin ki guda biyu da kuma gold company din can. Karin da aka yi sai ya saka tun a lokacin share din ki a lokacin ta fi ta mahaifin ki yawa a cikin both of the companies. Na saki baki ina kallon shi tun da ya fara har ya kai aya, sai kuma naji Daddy ya cigaba, na juya na cigaba da kallon sa shima, "It has been 18 years now da akayi making wadancan changes din, and a lot of things have also changed daga lokacin zuwa yanzu, Her shares have increased massively, while mine have reduced. A yanzu da nake muku magana Safiyya owns.……." Sai ya juya yana kallon daya mutumin da bai yi magana ba, mutumin ya bude takardar gabansa ya duba sannan yace "91%" ya rufe yana kallon na directly yace '"91% of everything" Daddy yace "yes, everything. Except for wannan gidan da muke ciki da motocin da muke hawa da kuma gidan mu na Abuja. Those are mine." Uncle Ahmad yace "yes, and she also have the sole ownership of The Oasis" mutumin da yayi magana da farko ya sake bude takardun gabansa yace "bayan The Oasis tana da gona guda uku da land guda biyu daya a Kano daya a Abuja and other personal items" Daddy yace "wadannan ba sune damuwa ba. Tunda sole ownership ne, damuwata shine wadanda muke tare da ita, I want to clear everything with the rest of my family members tunda ba'a san gobe ba. I want her, my wife and my other kids to know dan gudun samun rashin fahimta nan gaba, tunda..." Dariyar Mommy ce ta katse masa maganar sa, duk muka juya muna kallon ta, sai da ta gama dariyar sannan ta girgiza kai tace "wato wannan shine plan dinka kenan Adam, wannan ita ce sakayyar da kake gain zaka yi min kenan ko?" Daddy yace "mind your tongue Sa'adatu. Wanne plan kuma? I didn't plan any of this. Abinda Allah ya tsara mana dole shi zamu karba. I have...." .." Tace "you have always love Safiyya fiye da kowa da komai a duniya. You have never cared about me and the kids I birthed for you ballantana wadanda ba naka ba. Na dauki duk discrimination dinka saboda nasan cewa ita marainiya ce shi yasa kake bata special treatment dan kana gain kamar ni bana kulawa da ita yadda mahaifiyar ta zata yi mata. I have accepted that but I will never accept this. Ba zan taba yadda dan ciwo ya same kaka dauki komai da kake da shi kace nata ne ba. Mu kuma fa? Yayan ka maza kuma fa?" 13 13 10:12PM Yace "ba dauka nayi na bata ba. Dama nata ne. You already know. Tun mahaifiyar ta tana da rai kin san cewa ta bata dukiyar nan" Mommy tace yes, na san ta bata abinda take da shi a lokacin. But kaima ai da akwai naka a ciki, Na ka ma yafi nata yawa, Yaya za'a yi kuma ace min nata ya karu naka ya ragu bayan tare ake juya kudin, bayan tare ake raba ribar, Me yasa nata zai karu har ya kai 91% kai kuma naka ya ragu har ya koma 9%. Wanne irin lissafi ne wannan kamar ana so a nuna mana ba muje makaranta ba?" Daddy yace "Okay, tunda kin nemi bayani bara inyi miki gwari gwari. Nata yayi wannan karuwar ne saboda for over 20 years da muka hada kudi muka bude wadannan kamfanini bata taba ciran ko da kwamdala daga ciki ba. Sai ma karawa da akayi bayan rasuwar Safiya. Duk ribar da aka samu a cikin tsahon shekarun nan akan jarin ta ake kara mata. Ni kuma fa? Kudin nan da su nake yin komai da su nake yi muku komai. All the extravagant spendings, all the holiday vacations da ba kya yin watanni uku cikakku baki fita wata kasar ba daga cikin kudin ne, all the cars the latest gadgets, the bukukuwa duk a cikin kudin ne. All the kudin makarantar yara da ba kya so a saka su a kowace makaranta sai wadda tafi kowacce tsada, Mustapha da kika dage sai a kasar waje zaiyi karatu duk a cikin kudin ne. I have ER used all the money you are asking about to take care of you and the kids. Yanzu abinda ya rage min bai fi wanda zan rike ku zuwa sanda ciwon nan zai karasa ni ba. And that's idan kin ajiye wannan life style a gefe", Tace "okay, yanzu laifi na ne kenan? Laifi na ne that we know have nothing?" Uncle Ahmad yayi gyaran murya yace "Wadannan maganganun are private issues, muna tare da baki so let's calm ourselves mu gama abinda ya kawo su, in sun tafi sai mu tattauna sauran batutuwa" Daddy yayi ajjiyar zuciya yace "as you all know yanzu bani da lafiya, and it is a terminal illness da zai cigaba da cina till I am no more. So for now, every affair will be handed by Ahmad, abinda ya shafi dukiyar Safiyya da abinda ya rage min duk zai koma hannun sa zuwa sanda Safiyya zata mayar da hankali ta gama makaranta sai ta karbi abinta" Mommy ta cigaba da magana "wallahi da sake. Wannan abin da kuke fada abu ne da ba zai yiwu ba ko a mafarki. Chafdi" Babu wanda ya kula ta. Sai naga daya daga cikin bakin ya taso yazo gabana ya durkusa yana kallon fuskata yace "it is really nice to see you again Safiyya Adam. I knew and worked with your mother tun tana yin unique mix, da special awara" yayi murmushi "tun tana Safiya Haladu kafin ta koma Safiya Khalid, She is an amazing woman, And you are going to be an amazing woman too, I am looking forward to working with you as well" sai ya dauko wani card a aljihunsa yayi rubutu a bayan sa ya ajiye min a gaba na yace "this is my complimentary card, akwai duk information dina a jiki, ga kuma private phone number dina nan itama. You can call me anytime you want in kuna da wata tambaya ko wani legal issue concerning wannan maganar or any other one". Na dauki card din sannan na dago na kalle shi, for the first time tun da aka fara maganar nayi magana nace "thank you" ya mike ya koma inda yake ya sake zama. Mommy ta sake cewa "chafdi. Babbar magana" still babu wanda yace mata komai. Uncle Ahmad yace "akwai mai tambaya? Safiyya? Do you have any question?" Kowa yayi shiru babu wanda yace komai, zuwa can sai Mustapha yayi magana "ina da tambaya" uncle Ahmad yace "okay, muna jin ka" yace "duk wadannan lissafe lissafen ban gama gane su ba tukunna, I need a figure, how much is Safiyya really worth, In figure" uncle Ahmad yace "menene naka a ciki?" Daya mutumin ya fara bude takardu yana dubawa sai wanda ya kira kansa da lawyer yace "hold on. Shi waye mai tambaya din? because this is a security issue ba wai kowa akewa disclosing that information to ba" Mustapha yace "I am her brother, and I have the right to ask" uncle Ahmad yace "step brother. Her step brother" 14 13 10:12 PM Mommy tace "au gorin ya fara kenan, tun yanzu?" Daddy yace "just tell him. It is okay" mutumin ya karasa bude takardar sannan ya ambaci figures din da babu wanda bai tsorata ba a falon. Including uncle Ahmad. A fuskar sa na fahimci shima bai san kudaden sun kai haka ba. Falon yayi tsit na some seconds, sannan Mustapha yace "tashin sense" Mommy tace "wallahi da sake, wai an bawa mai kaza kai" Daddy ya zuciya "waye mai kazar kenan? Ke? Where were you sanda Safiya take neman kudin ta? Tare kuke soya awarar ko tare kuke shiga cikin kasuwanni sarin kaya? Where were you sanda take bi aji aji a makaranta tana musu tallan abaya? Tare kuke shara da wanke wanken ko tare kuke zaman shagon",. Tayi shiru bata ce komai ba. Hassan that was 15 years then ya daga hannu "ina da tambaya" uncle Ahmad yace "muna jin ka" yace "yanzu in muna son kudi wa zamu tambaya kenan? Daddy ko yaya?" Mommy ta daka masa duka a baya '"'banza sakarai wanda bai san me yake masa ciwo ba. Zaka rufe min baki ko sai na fasa maka shi?" OC Taron da aka fara shi cikin farin ciki da annushuwa, sai aka kare shi cikin mabanbantan yana yi. Sai da kowa ya tafi ya barni a falon a zaune ni kadai. Rewinding and unwinding maganganun da akayi. Daga nan kuma nabi Daddy har dakinsa na gaya masa cewa ni bana son abinda Ammi ta bani, na bar masa, ya cigaba da rikewa a hannun sa ya kuma cigaba da kula da mu baki daya. And he sat me down and talked to me. He told me about Baba Hadiza and Ammi and her siblings, he told me about it all. And then after two years and going through hell and coming back, I finally decided to accept what was given to me. Na sauke ajiyar zuciya sannan nayi taking first step a cikin falon, ga mamaki na sai naga duk sun mike tsaye irin mikewar da akeyi to show respect to manyan mutane. I held my head high and walked through them, zasu kai su ashirin roughly, na ga uncle Ahmad na kuma ga Mukhtar, sannan na ga Daddy. Na lura da mutane biyun da suka zo wancan zuwan but all the rest are new faces. Uncle Ahmad yayi wa Mukhtar magana "matsa mata nan kusa da kai ta zauna. Wannan shine mijinta. This is her husband" ya fada wa mutanen gurin. But I walked pass then na je gurin Daddy wanda shi kadai ne a zaune na zauna a kusa da shi. I wanted to create a very good first impression with them all. Ina son inji displaying confidence, smartness, intelligence and power to them. Bana son su ke kallo na a matsayin naive little girl. Kuma daga dukkan alama na basu wancan impression din. But even with all the displayed power, nayi kokarin gaishe su dan bana son power din tawa tayi overwriting tarbiyya ta. Daddy ne ya bude taro da addu'a, and he made the effort of including Ammie a cikin addu'ar tare da roka mata rahamar ubangiji, Daga nan sai uncle Ahmad ya fara kokarin yi min introducing mutanen gurin, Na girgiza kaina sannan na mike tsaye ina kallon su daya bayan daya nace "I am going to see them all uncle, amma ba'a nan ba. Zan ga kowa one after the other and talked to kowa privately in daddy's office" a fada ina nuna office din Daddy da yake da kofa ta cikin falon. I looked at Daddy and I saw the look da na bOd jima ban gani ba a fuskar sa, the look of pride. Naga chanji a fuskar Uncle Ahmad ya kama hannuna ya jani gefe "this is a bad idea Safiyya, wadannan mutanen ni na san su na san kowa, i have delt with them for years. ..." Nace "and now I am going to 43 learn how to deal with them too" yace "but at least take your husband with you" na juya na kalli Mukhtar da na fahimci ransa a bace yake nace "no uncle. I am going to do this alone. Ko Daddy ban ce masa ya shigo ba. Da ina son shiga da Mukhtar da ni da kaina zan ce masa ya zo". Na wuce shi na bude office din na shiga, na wuce can ciki na zauna akan kujerar Daddy sannan involuntarily na shafa pendent din Ammie da yake wuyana a hankali nace "alright Ammie, you want me to do this? I will do this", Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Thirty Seven: The Eyes Daya bayan daya suka ringa shigowa kamar yadda na bukata. Most of them sun haife ni, others sun girme ni sosai. Kowa d in ya shiga zai yi min introducing kansa da mukamin da yake rike da shi sannan ya bani brief breakdown of what has been going on a bangaren da yake rike da shi. Duk abinda suka fada min in recording a 43 karamar recorder din da na ajiye a gurin. Duk wanda ya gama kuma sai ince yaje ya rubuto duk bayanin da yayi min in written. Dalilin yin hakan shine dan in yi comparing said and written words din inga in zany detecting something. Abinda na fahimta shine kowa a cikin su yana kokarin cusa kansa ne a waje na, every one of them was trying to impress me. Some were even black painting others a kokarin su na buda wa kansu hanya a gurina, Wannan yasa nayi using dama ta, kowa idan ya gama sai in ce masa "naji dadin bayanan ka sosai, Kuma na fahimci cewa you are a good and hardworking person, I am glad you are part of my company. In babu damuwa ina son ka zama special adviser na, I want you to be my eyes and ears a duk inda bana nan, and I will appreciate it if you will report to me duk abinda kake gain ya kamata in sani" wanna kalaman suna saka su farin ciki sosai. And it mostly made them spill one or two information da da suka boye. Then kafin su fita sai in kara da cewa "aikin da na baka is confidential. Bana son kowa ya sani, daga ni sai kai". And that was how I tied them all to me. Kowa yana gain kansa a matsayin special somebody a gurina. And kowa yana yi min aiki secretly ba tare da sauran sun sani ba. A zama dayan nan na samu informations masu yawn da banyi tunanin samu ba. Sai bayan da na sallami kowa sannan kuma muka zauna da uncle Ahmad da barrister Umar da kuma daya mutumin da na fahimci shine account manager na. Anan aka chanja all the signatories zuwa signature dina aka cire ta uncle Ahmad, sannan yayi min handing over all the necessary documents and then muka shirya cewa zamu yi going on a tour a nuna min ko'ina and komai, Bamu fara fita a ranar ba saboda duk mun gaji, ga wata uwar yunwa da nake ji. Na samu dai a karshe suka ce zan iya tafiya, washegari zamu cigaba. Ina son in je inci abinci amma kuma ina son gain Daddy, ina son magana da shi. Sai na tafi dakinsa dan tun da na fara gain stakeholders din ya shiga dakinsa ya kwanta dan ba zai iya zama a cikin wanna hayaniyar ba. A kan gadonsa na same shi a kwance kamar mai bacci, na jima a tsaye ina kallon sa sai na juya zan fita dan bana son tashin sa, na kai bakin kofa kenan sai naji ya kira suna na. "Fiyya" ya jima bai ce min Fiyya ba, for months yanzu Safiyya yake ce min. Na juyo ina kallon sa sai yace "kun gama?" Ya gyada kai "mun gama da stakeholders din sun tafi. Dama taron is just to let them know I have taken over, so daga gurina zasu ke karbar duk wani directives" yace "then why do you have to see them one by one?" Nayi ajiyar zuciya na zauna a kan gadon a kusa da kafafuwansa nace "ina kokarin fahimtar su ne kawai, trying to know their personality saboda in fahimci yadda zanyi dealing with them" ya danyi gajeren murmushi "and you think you can understand their personality in one sitting?" Nayi shiru bance komai ba, yace "you did right, ba wai ina tuhumar ki bane ba, at least you have shown them power and instilled a bit of fear in them, kowa zai shiga taitayinsa. But I don't want you to be the boss that is fearful, I want you to be the boss that is loved. Ki saka musu son ki ta hanyar kyautatawa and at the same time ki zama strict with them" na gyada kai "insha Allah Daddy. Dama ina son ne in samu informations daga gurin su, and I got some" sai kuma nayi shiru, yana kallona yace "what information?" Na girgiza kaina deciding not to tell him now nace "I am not sure now. Zan dai kara bincike first" yayi ajiyar zuciya "there is something about information Safiyya. If you keep looking for it to tabbas you will get it. Ko dai ki samu true information ko kuma ki samu false information. Amma tabbas zaki samu. Matsalar zata fara ne idan kika samu false information. 20 14 10:09 PM Musamman idan kina da kudi. People will only tell you abinda suka san kina son ji dan su samu wani abu a hannunki. Very few people will look you in the eyes su gaya miki abinda suka san ba zaki ji dadin shi ba". Sai na gaya masa hanyar da na fara bi for now. "Kowa zai ke kawo min nashi report din, kowa zai saka wa kowa ido, so l am hoping I can get the truth that way" muka yi shiru ina tunanin ta yadda zan gaya masa mafi girman information din dana samu, sai dai kafin inyi magana sai naji yace '"I am sure sun fada miki something about Ahmad? What are you going to do with him? Wanne hukunci zaki yi akan sa?" Cikin mamaki nace "so you know what he has been doing? Ka sani all this while?" Yace "I already know the truth of it. An riga an gaya min ai ba tun yanzu ba. I even talked to him about it yayi min alkawarin zai mayar da kudin da ya dauka amma har yanzu bai mayar da kudin ba. Ya jima yana daukan kudade yana keeping it aside for himself. Just a month ago aka sake gaya min ya kuma daukan wadansu, and that was bayan kin amince zaki auri dansa". Nayi ajiyar zuciya nace "yanzu ai ba zai sake dauka ba. Yanzu bashi da damar daukan ko kwandala kuma" yace "shi yasa ya dauka ai, saboda ya san in kika karbi aikin ki ba zai samu damar dauka ba. Yanzu me zakiyi akan wadanda ya 9? dauka already?" Nace "I don't know Daddy, abinda ya sa na shigo gurinka kenan, Nasan kullum in zaka yanke hukunci kana tunanin abinda Ammie zata yi, me kake tunanin zata yi idan ita ce a matsayi na?" Yayi shiru yana tunani sai yace "your mother had been a great woman. Ta iya zama da mutane sosai. Tana da dabarun da take amfani da su ta juya mutane ba tare da sun san tana juya su ba" yayi murmushi "just like yadda kika fara yanzu, you are so much like her" nayi murmushi nima. Ya cigaba "she warned me about Ahmad, she said money is sometimes evil and can change people's behavior, Ahmad ya bautawa business dina tun lokacin da shago daya kawai nake da shi, shi nake bari yana jire min shagon a lokacin da ni kuma nake pursuing higher ambitions. Yes, tun lokacin yana kara kudi akan kaya ya siyar dan shima ya samu ta sa ribar kamar yadda duk masu irin wanna harkar suke yi, amma bai taba daukar min kudi ba. As the shop turned into shops and then into an industry he started becoming greedy and possessive. I think mistake din da nayi making with him shine na danka masa ragamar komai a lokacin da na fara rashin lafiya, I did that to strengthen trust dan in na bar ku ya kyautata rikon da zai yi muku, but it made him more greedy and more possessive. Yaji zakin dukiyar baya son rabuwa da ita, shi yasa ya dage akan ki auri dansa tun farko, he thought auren zai hana ki karbar dukiyar daga hannun sa, after you refused the offer sai ya fara daukan kudin yana ajiyewa for himself, daga baya kuma you chose auren dan nasa, he then became comfortable cewa ko kin karba daga hannun sa dan sa zaki saka a kai ko kuma shi ki barshi ya cigaba da juyawa. He was devastated today after you took it from him and cast the son aside" yayi shiru yana kallon na, waiting for me to say something. 100 Nace "that was why ka nuna baka son zabar Mukhtar da nayi?" Yace "yes. If I was the one given the choices I would have chosen Mustapha, idan kuma aka cire Mustapha daga cikin options din gwara in zabi Abdul din da ban gama sani ba sosai akan Mukhtar" Na girgiza kaina feeling stubborn "Daddy ba ka san Mustapha ba, the Mustapha you know is different from the one I know. And I don't think Mukhtar is as bad as you think. He is my friend. Kuma ba lallai ne ya san plans din baban sa ba". Ya gyara kwanciyar sa yace "you are wearing your mother's clothes and acting 3 83 like her. But you are still a child", Na bar part din sa na shiga cikin gida da niyyar in ci abinci in huta, a raina sam na manta da Mukhtar yana gidan saboda gajiyar da nayi, Ina shiga na bada umarnin a kai min abinci dakina dan ba zan iya zama a dining in ci ba. 23 5 10:09 PM Kai na tsaye na bude kofar dakina na shiga na ajiye jakar hannu na sannan na cire mayafi na shima rataye shi, na tsaya a gaban mirror ina kokarin cire dan kunne na kawai muka hada ido da shi a kwance akan gado na. Na firgita saura kadan in kwalla kara sai kuma na rufe bakina da hannu na gudun kiran attention din mutane. Ya tashi zaune yana kallona yana dariya "I always knew ke farar kura ce saboda toro" na juyo ina kallon sa har lokacin iiki na yana karkarwa "me kake yi anan Mukhtar? Menene hakan? Me yasa zaka shigo min daki ba tare da izini ba?" Ya tashi tsaye "gurin wa zan nemi izinin shiga dakin matata? Koke baki da damar hana ni shigowa dakin nan a yanzu. Abba yace anan zamu kwana so I decided ni anan zan kwana" ya fada yana nuna gadon da ya tashi daga kai, ©️? Na dauki jaka ta tare da mayafi na nace "'bani da ikon hana ka shigowa dakin nan ka ce ko? Amma ai ina da ikon bar maka dakin ka zauna a cikin sa kai kadaj" na fada ina yin hanyar fita daga dakin, Cikin taku biyu ya kamo hannu na ya dawo dani baya, saura kadan in fada jikinsa nayi regaining stand dina, raina a matukar bace na nuna shi da daya hannun nace "ka sake ni Mukhtar, I am very serious" ya saki hannun yana kallon fuskata "why are you so difficult ne. Relax. You are so tensed. Ba wani abu zanyi miki ba I just want to sit down with my wife and have a talk" Nace "zaka fitan ne ko ni in fita. I just want to be alone ne yanzu. I want to rest, na gaji da yawa". Maimakon ya fita sai ya ja kujerar gaban mirror na ya zauna yace "a problem shared is a problem half solved. Zauna ki gaya min abinda ya saka kika zama this edgy" na zauna a bakin gado ina kallon sa "I don't want to talk about it, I just want to be alone and think about it" yace "okay. Pretend kamar bana nan. Kiyi harkokin ki kawai. I will just sit here and enjoy your presence". Nayi shiru ina kallon sa bance komai ba, yayi murmushi "you were about to undress before you saw me. Continue from there" na girgiza kaina "ban san sanda ka zama haka ba Mukhtar. You were decent a sanin da nayi maka. And I like the former version of you better" yace "nima haka, I like the former version of you better, The former Fiyya that was always free and kind with me. Not this one da take nuna kamar ta tsane ni". Ban bashi amsa ba aka yi knocking aka shigo, yarinyar da na ce ta kawo min abinci ce, tazo ta kama jera flasks din abinci nace mata "ni fa ba cewa nayi ki cika min daki da abinci ba, a plate kawai nace ki zu bo min wanda zan ci ki hado da drink da spoon ki kawo min" tace "Mommy ce tace a kawo miki gabakidaya ki zuba wanda kike so" nayi ajiyar zuciya sannan nace ta zuba min shinkafa da miya, sai kuma na kalli Mukhtar da yake zaune still ya zuba min ido nace "zaka ci abinci?" Yace "I thought ba zaki yi min tayi ba" yarinyar da take zuba abincin ta dan tsorata saboda bata lura yana dakin ba sai muryar shi kawai ta ji. Nace mata '"'barshi kawai, tashi kije, in ya gama kya dawo ki dauke, ta tashi da sauri ta fita tana juyowa tana kallon shi. Nace "kaga ka tsorata yarinyar mutane, yanzu zata je tana wondering me kake yi anan" yace in ta tambaya sai a bata amsa, a gaya mata dakin matata ne. Na dauki plate din da ta fara zuba min abincin na karasa zubawa sannan na koma na zauna na fara cin abinci na saboda yunwa da nake ji. Ya sauko daga kan kujerar shima ya zuba abincin ya fara ci sannan yace "So, how is he?" Na ajiye spoon din hannuna nace "how is who?" Yace "The boy, what name kika bashi ne wai? Dole in zaki cike information din sa acan sai kin saka suna, so definitely kin saka masa suna. Wanne sunan kika saka masa?" Nayi shiru ina kallon sa sannan nace "why do you want to know?" Ya dauke idonsa daga nawa ya daga kafada yace "is it now a crime idan mutum ya nuna damuwa da abinda ya shafi matar da yake so? Yanzu na gama gaya miki cewa you are edgy, abu kadan yake bata miki rai" na cigaba da cin abinci na '"'I don't want to talk about him" yace "okay, shikenan" sai kuma ya chanja topic ya fara yi min maganar gyaran gidan da yake yi da lefen da yake hadawa. 22 10:09 PM "Da tuni duk an gama komai ba dan Mommyn ki ta kwafsa mana ba. Banga abinda zaki anan wanda ba zaki yi a can ba. Sai ma abinda zakiyi acan wanda ba zaki yi anan ba" ya karasa yana kokarin hada ido da ni. Nayi kamar banji me yake cewa ba na cigaba da cin abinci na har muka gama gabaki daya, Sai ya dauko wayarsa ya dawo kan gadon ya zsuna a kusa dani "I want to show you the new design da aka chanja wa kitchen din nan, you will like it na sani, na san how much kike son kitchen" na karba nayi scrolling through pictures din, ban wani gane designs din sosai ba dan kaina ciwo yake yi na gani sosai. Na mika masa wayarsa '"ni fa ba gane wa nake yi ba wallahi. Na gani later. I just want to rest yanzu" ya mike "okay, bara in barki ki huta. We will talk later". Har zai fita sai ya ga wayata a ajjiye a kusa da jaka ta, sai kawai ya saka hannu ya dauka "you need to change this phone" ya fada yana juya ta a hannun sa, nayi shiru ban ce komai ba dan ni kawai so nake ya fita ya bani guri, sai kuma naji yace cikin murya mai kaushi "who is this?" Na juyo na kalle shi sai ya nuno min hoton screen din waya ta. Na dauke kai nayi kamar ban gani ba na fara kokarin gyara gurin da muka ci abincin "who is this na ke tambayar ki?" Ya fada yana doso ni da wayar a hannunsa "oh ba zaki bani amsa ba?" Na fara jin tsoron yanayin sa, he looked like he did sanda yake gudu da mu a mota, na dauke ido na daga cikin nasa "you already know who is that, kuma hoton ya jima a screen din I didn't get the time to change it" "you didn't get the time to change it or you don't want to change it? Whatever the case, I will change it for you" yana fada sai yayi jifa da wayar, ta daki bango ta fado kasa ta tarwatse, Na mike tsaye ina kallon sa "you broke my phone" na fada cikin mamaki, ya wuce ni ya je inda wayar ta fadi ya saka kafar sa me sanye da takalmi ya take wayar, yace "yes I did. And this is the last time da zan kuma gain anything related to that guy a gurin kj" na tsaya kawai ina kallon sa, ya dawo ya tsaya a gabana, blocking my view with his big body, yace "ina sonki matukar so Safiyya. Na bi bayansa da kallo har ya fita, ina jin raina yana kara baci. Ba wai wayar da ya fasa ce damuwa ta ba, I was surprised and concerned that he had that kind of temper. What if nan gaba ba waya zai fasa ba? Na karasa inda wayata take a ruguje a kasa na durkusa ina tattare ta, ina tunawa da cewa Muhammad ne ya siya min ita, tare ya siya mana iri daya ni da shi. Washegari da safe ina tashi sai ga sako an kawo min any wrapping dinshi, Na ksrba na bude sai ga sabuwar waya a ciki with an "am sorry" card, ban karanta rubutun ciki ba dan na fahimci daga gurin wanda yake, a bayan card din yayi rubutu, "Am sorry darling. I promise to never loose my temper again" Na mayar da card din cikin wrap din na ajiye. Su Hassan suna shigowa na aika su suka siyo min wata wayar dan nasan za'a yi ta nema na. Har Mukhtar ya koma Abuja ban kara yi masa magana ba duk kuwa da bada hakurin da yayi ta yi min. Satin ya zo min cikin sauri sosai dan kullum kusan a waje nake wuni. We had an extensive tour tare da uncle Ahmad wani lokacin har da Daddy da Mukhtar ko Mustapha. Sai a lokacin na kara fahimtar dalilin da yasa Daddy ya kafa min takunkumin yin karatu mai zurfi dan ni kaina sai da naji na raina ilimi na, abubuwa da dama in anayi min bayani sai inji ban gane ba, amma bana nuna ban gane din ba sai dai kawai inyi taking note, duk abinda ban gane ba kuma bana yanke hukunci akan sa sai na je gida nayi research akai kuma na tambayi Daddy ya kara yi min bayani sannan in yanke hukuncin da nake ganin ya dace da abin, Ina lura da yadda uncle Ahmad yake cigaba da kokarin cusa Mukhtar a duk abinda muke yi, ina kuma lura da yadda shi Mukhtar din baya so, shi yayi concentrating ne akan gain mun shirya yayin da ni kuma na ki bashi damar hakan. Har kuma muka gama tour din yi wa uncle Ahmad maganar abinda ni da shi duk mukasan yayi ba saboda har lokacin ban gama yanke shawarar hukuncin da zan dauka ba. 18 10 10:09 PM Bayan sun koma kuma sai nayi concentrating on revamping the whole industry, akwai chanje chanje da dama da nake son making wadanda nayi magana da Daddy kuma ya amince. Kullum ina cikin meeting, duk da dai wadanda na gayyata gida suke zuwa su same ni amma still kullum a gajiye nake and that gajiya helped me a lot wajen rage tunanin abubuwan da suke gudana a rayuwata. Tunani biyu ne yafi damuna idan nazo kwanciya bacci, na Muhammad dana Junior. I always wondered how they are doing. How they are coping with their fate. A raina nasan Junior is doing well but I was not sure about Muhammad. Sai da na gama da tour din na kuma yi setting a lot of things in motion sannan kuma na zauna meeting da family na, I told them straight forward "daga yanzu a gidan nan there will be no more free money. Every one will have to work to take care of himself" Mommy tace "ban gane ba, aiki zamu ringa yi miki kenan a gidan?" Nace "Mommy ai ni ban isa ince zaki yi min aiki ba, ina magana ne da samarin gidan nan" tace "twins dai karatu zasu yi, karatun zasu fasa su zauna yi miki aiki?" Na tara tattaro patience dina dan kar in gaya mata magana nace "bani za'a yi wa aiki ba, kowa kansa zai yi wa aiki. Mustapha, zan baka list of vacant positions da muke da su in the company sai ka zabi wanda kake so and the job will be yours" ya daga hannu "] don't need it. Na riga nayi submitting cv na zuwa gurare da dama, I will soon get a job" nace "your choice" sai na juya gurin twins nace "kai Hassan tunda harkar engineering kake sha'awa zaka yi joining team of engineers din mu in the factory, zaka fara aiki da su kana koyon yadda suke gudanar da aiyukan su kuma kana yi musu kananan aiyuka" Mommy tace "I don't believe this, laburanci zaki tura shi? Kanin naki?" Ban bata amsa ba na juya kan Hussain "kai kuma tunda naga you have daddy's business mind, you will join the marketing department, kai ma zaka koyi aiki za kuma ka taya su aiki, Zakuyi aikin zuwa sanda zaku samu admissions and even kun fara karatu we will still find a way for you to continue your job part time zuwa sanda zaku kammala karatu then you will take it full time" na bisu da kallo naga yadda duk suka yi shiru suna kallo na, nace "any question?" Hassan ya daga, nace "dama na san kai zaka fara magana, menene tambayar ka?" Yace "nawa ne salary din?" Daddy da yake zaune yana jin mu yayi dariya, Hussain yace "yaushe zamu fara aikin?" Nace "as soon as you can get[07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: Daddy da yake zaune yana jin mu yayi dariya, Hussain yace "yaushe zamu fara aikin?" Nace "as soon as you can get yourselves to your various departments. You will discuss your salaries with the heads of your departments" suka juya suka kalli juna sannan suka yi murmushi, Hassan yace "shagali, duniya sabuwa" Daddy yana kallon Mommy yace "see? They are happy. This maybe the best decision da aka taba making a rayuwar su" amma Mommy still kamar abin bai yi mata dadi ba, ita a son ranta shine a nemi makarantar da tafi kowacce tsada a Nigeria ko kuma wata babbar makaranta a waje a saka su, a kuma cika musu accounts din su da kudi, Sai ta juyo tana kallona "saura ni kuma, a wanne department za'a saka ni?" Nayi murmushi duk da na san bakar magana take gaya min nace "ai ke Mommy Allah ya riga ya baki aikin ki, permanent aiki, aikin kula da Daddy, all your expenses will be taken care of, duk abinda kuke bukata a gida ko na personal use din ku will be provided" naga fuskar ta tayi relaxing alamar hankalin ta ya kwanta, sai na kara da '"but not in cash. Except when necessary. Duk abinda kuke bukata will be provided directly". And that was a story for another day. Tafi sati tana mita akan hakan. But I stood my ground. Da taga ba zan chanja shawara ba, ta kuma tabbatar Daddy baya na yake bi sai ta koma shirye-shiryen biki, ta rubuto min dogon list na abubuwan da za'a siya da kudaden su and I was like "what?" Na fahimci ita bata jin wahalar ambatar kudi komai yawansa, ni kuma yanzu da na fara wannan role din kudin da nake bukata na siyan abubuwan da za'a bukata ne gurin gyare-gyaren da na tsara za'a yi wa factories ne, Da nace mata no sai ta tafi ta kai kara ta gurin Daddy.A dole nayi mata signing taje ta karbi kudi ta cigaba da hidimar ta, 22 10:09 PM Duk wani abu da za'a bukata a gida ta siya, har abubuwan da ba za'a bukata ba ma ta siya. She spent more money a kayan dakina then she did a kayan dakin Safina. Kullum kuma in ta je hidimarta ta dawo ta ringa loda min karkacen magunguna kenan. '"Wannan da madara zaki ringa damawa kina sha, wadannan kuma su zaki mayar ruwan shan ki kiyi ta sha daga yanzu zuwa bikin. Wanna kuma a tsarki ne duk da dai cs akayi miki amma dole sai anyi miki gyara sosai" in ta bani sai in nemi deepest corner of my room in ajiye, sai na shan ne takan takura min ta zaunar da ni ta ce sai na sha "dan ke nake so inyi miki wanna gyaran ba wai dan wancan mara kunyar yaron ba. Kin san se da na korawa uwar nan ta sa bakaken maganganu wanna zuwan da nayi Abuja? Naje zan karbi key din gidan nasa zamuje muyi aune aune, matar nan tana ta wani kumbura kamar an saka mata yeast, ni kuwa na gaya mata boldly cewa dan ta da ubansa su suka kawo kansu kuma suka dage sai anyi, su suke nema ba mu ba, in tana ganin ta isa kuma ta hana gani, Akwai da yawa suna jira suyi replacing dan nata" tayi shiru tana jira in yi magana, jin bance komai ba sai ta kara da "Allah ne kadai ya san me suka yi miki ma har idonki ya rufe kika zabe shi, Dan ni ban yarda da wanna lamarin ba". Daga nan kuma sai ta bani labarin Safina. '"Naje gidan Safina. Ni fa wannan auren nata ban yarda da shi ba har yanzu. Kin ga yadda yarinyar nan ta kare ta lalace kamar ana yankar naman ta ana ci? Nayi ta tambayar ta kuma kin san halin Safina da hakuri ta ki gaya min komai, in na tambaye ta sai tace babu komai. Ni ban san yadda zanyi ba wallahi. It breaks my heart to see her like that. Wannan mijin nata ni sam ban yarda da shi ba, har yanzu hankali na yaki kwanciya da shi". Da naga ba zata daina zancen Safina da mijinta ba sai nayi excusing kaina na tafi daki dan bana son jin duk abinda ya shafe su, but through out that night I kept wondering what was happening with them. Saura sati biyu biki aka kawo lefe, Daddy ya gaya musu baya son attention dan haka babu mutane sosai kuma da yake abin na gida ne masu kawowar dai sune kuma masu karbar. Aka gama ganin kayan anan sannan Daddy yace a zuba su a mota a kai su Abuja in za'a je jere gidan Mukhtar sai a tafi dasu kawai can tunda ba amfani zanyi da su anan ba, Amma duk da haka sai da Mommy ta dauki set din akwati daya cike da kaya tace na rabo ne. "'Yan uwa zaa rabawa da abokan arziki. Ke menene shire shiryen ki ne? Ni ban ga kina yin dinkuna da siyayyar kayan fitar biki ba, ki kira Safina ta hada ki da tailor din da yayi mata dinkunan bikin ta, na ga ya iya sosai" Na girgiza kaina "ni na gaya muku babu abinda zanyi Mommy, ba zan rasa kayan da zan saka ranar kai amarya ba. Shikenan" ta girgiza kai "ba zai yiwu ba ai ba auren dole ake yi miki ba, ke kika zaba da kanki" haka ta saka ni na sake fitar da wasu kudaden na bata tayi min dinkunan fitar biki. Mun dan shirya da Mukhtar na fara daukan wayarsa bayan na tabbatar cewa ya gane kurensa, sai dai kuma bani da tabbas din cewa he won't be that violent in the future. Ten days to biki. Already Mommy ta gama tsare-tsaren ta, za'a yi kamu anan gidan mu sannan zata kama event center tayi mother's eve, shikenan sai a tafi Abuja a sake yin wani yinin acan wai Saboda su Hajiya da sauran kawayen ta da ba zasu samu zuwa nan ba, Sai kuma akai amarya, Ni dai ina ta jin ta ban saka mata baki ba. A ranar I had a very long meetings with engineers din mu akan sababbin machines din da za'a siyo, bamu dama ba sai late afternoon sannan na samu na shigo gida naci abinci nayi wanka na chanja kaya into pajamas da niyyar ba zan sake fita daga daki na ba sai safiya. Sai da na gama komai na zauna sannan na dauko waya ta da niyyar duba wani message da nake saka ran za'a turo min. Sai dai ina budewa na ga message daga Abdul. Nayi murmushi na bude message din and I saw a lot of pictures wadanda tun kafin in bude su na fahimci na waye. Abdul din ya rubuta "mun girma fa. Getting big and ready for big brother's wedding" na tuna Mommy ta gays min an saka bikin sa za'a yi two weeks after mine. 23 10:09 PM Nayi murmushi sannan na bude pictures din. Da gaske yayi girma din his skin looking smooth, babu wrinkles irin na premature babies, fuskarsa ta ciko tayi kiba har da kumatu, his facial features more pronounced than sanda aka haife shi, yanzu kamannin sa da Daddy sun ragu ya zama yana looking more like me than Daddy, Hotunan suna da yawa, har da short videos of him smiling, wadansu pictures din a asibiti wadansu kuma a gida. Wadansu tare da Abdul wadansu tare da Aunty Hajjo. Daga alamu Abdul is very fond of Junior. Ina cikin scrolling nazo kan wani picture, anyi zooming fuskarsa sosai and he was calm and looking directly at the camera, with a serious face. And my heart stopped for a second. Na kife wayar tare da dafe kirjina ina jin wani irin ciwo a cikin zuciyata. Sai da nayi ta ambaton sunan ubangiji sannan na sake daukan wayar na kuma kallon hoton. His eyes looked exactly like his. Kamar shine yake kallo na whenever he is serious. Na sake ajiye wayar tare da rufe fuskata da hannayena guda biyu "it is not him. It cannot be him" amma kuma naji har a cikin bargon jikina that it is truly him. Na bude fuskata ina jin hawayen da na yi alkawarin a daina suna betraying dina, sannan wani irin rage yana mamaye zuciyata da duk kan bargon jikina, Na sake daukan wayar ina cigaba da kallon hoton sannan na je na lalubo wasu pictures dinsa da ya turo min just a week ago. I chose wanda ya kalli camera sosai and looked serious, sai na hada su side by side da hoton Junior and the eyes looked exactly the same, kamar na mutum daya. Tun bayan da na haifi Junior na dawo Nigeria, it looked as if komai ya wuce, babu wanda yake maganar babu wa da yake kokarin bi mini hakkina. Hatta Daddy ma tunda na bar asibiti bai sake yin maganar ba, kokarin sa kawai ya aurar da ni ya binne maganar abin kunyar da yake ganin na jawo mana. I have been trying to bury it for the time being as well. Amma ba wai na manta bane ba, it was something that can neither be forgotten nor forgiven. He took my life away from me, and doomed Junior's life. And now, I will take his life as well… Amma ta yaya zanyi hakan? Junior's eyes looking like his is not enough proof na cewa shine babansa. Ko da court zan je ba zasu karbi wannan a matsayin shaida ba dan yaya suna iya dauko wani abu na dangin su na can nesa ma ballantana shi da yake first cousin dina, I need to have something better than that. Zan iya samun another shaida if I can get to see him naked. If I can see the marks I need to have something better than that. Zan iya samun another shaida if I can get to see him naked. If I can see the marks Naji zuciya ta tayi min wani irin nauyi when the realization hits me. Tunda abin ya faru nake karar da dare na da rana ta gurin gaya wa ubangiji and begging him to find a way out for me, and he chooses MUKHTAR as my husband because He knows that sai na aure shi sannan zan ga abinda nake nema. Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:42 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Thirty Eight: A Night to Remember Na cigaba da zama a guri daya kamar statue, ina jin bacin rai yana cigaba da mamaye dukkan ilahirin jijiyoyi da bargon jikina. Mukhtar has always been a friend to me, more like babban yayan da Mustapha ya kasa zame min. I always run to him for consolation tun sanda ina yarinya, he has always been the first person da nake nema in ina bukatar taimako ko a way out of my mischief. He is one of the few people da nake feeling comfortable around, nake iya being myself around. Ko gidan su naje da shi nake wasa instead of su Salima da Salim da suke kusan mate dina. Da na kara girma kuma in dai naje Abuja to ya zama driver na, yawo lungu da sako na Abuja babu inda baya kaini. Zai iya siya min abu bai siyawa Salima ba ballantana Safina da dama can ba shiri suke yi ba. Ko da wasa ban taba tunanin shine ba.... 1 have always thought Mustapha ne, idan kuma ba shi bane ba sai dai wani can daban. Wani wanda ba Muhammad ba, Duk da yadda Daddy ya dage wajen kokarin convincing dina cewa Muhammad ne amma ni na san ba shi ba ne ba saboda na farko Muhammad yana sona, he could never have hurt me that way. Idan ma har yana son aikata haka da ni he could have easily seduce me or maybe emotionally blackmail me to get it tunda ya san ina sonsa but not rape me, not in that cruel way. *. *. **. *. Muhammad ya jima yana ta putting pressure on me about going next level with our relationship kusan tun a shekarar mu ta farko a makaranta. Tun ina chanja topic in yana yi min maganar har na fara yi masa karya hakan kuma ya sa ya kara damuwa, saying ba son shi nake da gaske ba. On the other hand Daddy have warned me strictly akan maganar saurayi tun farkon shiga ta jami'a. "idan na ganki da saurayi Safiyya, you are living that school ko zaki yi kukan jini. You are there to study and become what your mother sacrifices a lot for you to become not to be distracted by something not important", Shi bai san saboda saurayin ma naje makarantar ba, Yadda yake tsaurara min akan kar inyi saurayi ne ya saka da kansa ya dauke ni daga gidan uncle Ahmad ya mayar da ni hostel a lokacin da Mukhtar yace yana so na. "karatu zaki yi ba soyayya ba. Lokacin da zakiyi aure zai zo, and even then, zan saka ido in tabbatar da wanda zaki kula ya chanchanta kafin in barki ki kula sh'" shi yana gain ya dauke ni daga gurin Mukhtar, not knowing gurin wani saurayin ya kaini da kansa. And later after he broke the news of my mother's gifts to me, sai na fahimci dalilin da yasa ya dage akan karatu na kuma ya tsaurara akan maganar saurayi, amma ni a tunani na maganar sa bata da tushe, I can manage my wealth and study at the same time, a gefe kuma ina soyayya da Muhammadu na. Right? Amma bai yarda ba, ya kara buga min warning akan soyayya. "Especially now that this news is out, you will find it hard to differentiate between true love and fake love". Naso inyi masa bayani ai wanda nake so bai san duk wannan ba ballantana yayi faking, but na san yana jin labarin already ina soyayya zai raba mu. A lokacin ne kuma fake love din ya fara bayyana, Mustapha ya chanja toward me and became kind and soft spoken and a karshe ya gaya min wai yana so na. I laughed out loud when he said it. And I understood more of what Daddy meant. As I continued hiding Muhammad, our relationship grew stronger and stronger each day yadda ni kaina na fahimci auren na ke so ba karatun ba. And Muhammad ya cigaba da takura min da zancen inyi introducing dinsa a gida, tun ina yi masa karyar Daddy baya nan har na gaji na samu Mommy da maganar, a tunani na ko zata iya lallaba Daddy ya ga Muhammad ko yaga iyayen sa just to prove to him cewa ba yaudarar sa nake yi ba, in yaso sai in cigaba da karatu na kamar yadda Daddy yake so. 33 11 12:01 AM Amma sai Daddy ya kira ni yace "I will go to your school and withdraw you tunda ba karatun kike ba, sai in sama miki makaranta a waje ki tafi can kiyi karatun, dama ke kika nace wannan kike so" da kyar na samu na lallaba shi ya hakura ya bar ni in cigaba da karatun a nan bayan nayi masa alkawarin babu ni babu kula wan saurayi har sai nayi graduating. And then two years into my studies, muna exams din gama level two zamu shiga three, I decided to take a bold step in kawo Muhammad gidan mu duk da babu amincewar Daddy sai in ga yadda drama din zata yi unfolding. anar birthday din Muhammad ne, he was turning 27 years. Ranar ne kuma Daddy zai shigo Abuja shi da Mustapha. Ya kira ni ya gaya min cewa ni zanje airport in dauko su idan sun sauka. Saukar dare zasu yi. And I planned on spending time with Muhammad har zuwa lokacin saukar ta su sannan sai in tafi da shi airport din mu dauko su Daddyn tare. I was scared of what will happen amma kuma I was determined. So I took Muhammad to the restaurant and celebrated his birthday, a gurin kuma nayi masa alkawarin a ranar zai ga mahaifina. He was so happy... I was so happy……. And then as muna tsaka da cin abincin mu, his phone rang, ya dauka "hello, who is this?" Sai ya ajiye "bana ji..... .." Nace "hope it is not important" ya kalli wayar "new number, ban san waye ba", Muka cigaba da magana, and he was already planning on yadda zai siye Daddy na da dadin baki, "He is a difficult person, I am not sure idan zai yarda da dadin baki" ya daga kafada "I am use to difficult people, Don't worry, he will like me ko da baya so, But I suggest you go alone to the airport ni kuma sai kiban address din gidan da zaki kai shi sai inje in jira ku a can. He may not like seeing us together a titi" Na gyada kai, agreeing with him. Wayar sa ta sake kara yayi ignoring nace "ka dauka, maybe it is important" ya dauka wayar "bana ji ai, kamar network din is bad hear" ya saka a kunnen sa "hello?" Sai kuma ya mike tsaye yayi min murmushi tare da yi min alamar zai je waje da hannun sa, I nodded and smiled back at him and watch as he goes out. Yana fita na dauki fork dina na cigaba da cin abincin gaba na ina lissafin yadda haduwar shi da Daddy zata kasance da challenges din da zan fuskanta. Na saka abincin a bakina kenan kira ya shigo tawa wayar, na kalli screen din and I saw an unknown number, without thinking about anything na dauka na saka a kunne na "hello?" And I heard a voice that sounded so much like Mustapha's "Fiyya! Kina ina? Mustapha ne. Jikin Daddy ya tashi mun tafi dashi asibiti. Hurry up" Na mike da sauri gabaki dayan jikina yana daukan karkarwa "hello, yaya Mustapha? Mustapha?" But watakara kawai nake ji on the other side ban kuma jin magana ba. I cut the call and called again aka kuma dauka but still bana ji "Mustapha? Kun shigo gari? Kuna ina?" Still static, and then another sound "hurry up" na saka hannu na dauki handbag dina cikin sauri nayi waje a hankali ina magana da kaina cikin tashin hankali "Daddy. ..... • Wayyo Daddy na...... Wayyo Allah na….... " Nayi waje a rikice hawaye yana bin fuskata. Ina fita na cigaba da kokarin trying number din da aka kira ni da ita amma kiran baya tafiya, zuwa lokacin sam na manta ma da cewa tare muke da Gidado ballantana in neme shi gabakidaya hankali na yayi kan mahaifina da yake fama da rashin lafiyar da already likitoci suka fara lissafa masa lokacin da ya rage masa. Da sauri na doshi mota ta babu kowa a gurin motar sai securities da suke daga can bakin gate, na san asibitin da Daddy yake ganin likita in yana gari, sai da naje gaban motar na fara kokarin bude ta sannan na lura da fork din da nake cin abinci da shi a hannu na, ban san ma na fito da shi a hannu na ba, Ina zaro key din motar naji saukar hannu a fuskata ya toshe hanci da bakina a lokaci daya, toshe hanci da bakina a lokaci daya, tunanin da ya fara zuwa kaina shine kidnappers ne, wani matsanancin toro ya shige ni, zuciya ta ta buga da karfi making my whole body weak, duk da haka sai da nayi kokarin fighting amma sai aka hada ni da jikin motar aka matse sannan aka kara matse min hanci da baki aka hana ni 25 6 3 12:01 AM numfashi, weakening my body more. I started to paint, and I felt tsining allura yana huda fata da tsokar kafada ta, and then I lost consciousness. Tsananin azabar zafi ne ya farkar da ni. Zafin daga kasa na yake farawa sannan yay vibrating through dukkan gabobin jikina, blocking every line of thought, destroying everything that made me who I was and stealing every dream I ever had. The strokes did not only took my virginity, they took away my life. An dare min idanuwana very tightly, babu abinda nake gani sai duhu. At first pain din da duhun ba su barni na gane abinda yake faruwa ba, I later realized what was happening and I was devastated, I started fighting, trying to hit the man above my with the little bit of energy that I had, at the same time kuma ina kokarin bude idona but allurar da aka yi min har lokacin ba ta bar jikina ba, and also karfi na was no match for karfin namijin da yake tare da ni. A cikin kokawar da nake yi ne hannu na ya sauka akan something metallic a gefe na, ina dauka na fahimci fork ne from it's shape, fork din da yake hannuna lokacin da na fito daga restaurant din. In seconds na dauka sannan da dukkan karfina na soka wa wanda yake tare da ni. I didn't think zai huda jikinsa but it did, yayi sauri ya matsa daga jikina and I felt his blood on my hand. Nayi sauri na fara kokarin kunce daurin da aka yi wa idona duk kuwa da zafin da nake cigaba da ji a kasana. But an saka karfi sosai gurin yin daurin and my hands and my whole body was shaking violently, amma kuma a lokacin babu abinda nake son gani sai fuskar wannan azzalumin, fuskar wanda ya dauki rayuwata, Amma kafin in samu damar kunce ko da dauri daya ne he came back and held both my hands in one of his hands and I felt another allura pierced the flesh of my arm, " will kill you!" Na fada "I will kill you" na maimaita and then I lost consciousness again. Sanda na sake farkawa I was alone, lying at the back seat of my car completely dressed. Jaka ta, wayata, and mayafi na all together akan seat a kusa da ni. Motar a kunne, with the AC on. Nayi kokarin mikewa zaune amma gabakidaya jikina ciwo yake yi, kafafuwana har karkarwa suke yi. Har lokacin ina jin alamar allurar a jiki na, dusu dusu nake gani, hatta kunnuwa na jin su nake yi kamar ruwa ya shiga ciki ya toshe su. Sannan ga bakin cikin da ya toshe makogwaro na ya hanani numfashi. Na kama kujerar gaba for support sannan na mike zaune da kyar jikina gabaki daya yana karmarwa, kokari kawai nake yi in samu in leka waje ko zan ganshi, ko zan ga wanda ya dauki rayuwata. Duhu na gani a wajen, na kalli agogon cikin motar naga 12:30 na dare. Wajen yayi duhu sosai except for the street light, da street light din kuma na gane inda nake, layin gidan mu ne, just two houses away from gidan mu, Na dauki waya ta na duba and I saw several missed calls daga Muhammad da Daddy da kuma Mustapha, Mustapha, I was 70% sure it was Mustapha because of the encounters I had with him before that, because of his name and his voice that was used, and because of how him and his mother reacted ranar da Daddy yayi revealing my wealth. And also because of how they treated me before su san kudin da nake da shi and after sun san kudin da nake da shi. Na bude kofar motar na fito zuciya ta tana tafasa, duk da ban ga fuskarsa ba but I was sure Mustapha ne. Babu abinda nake so a lokacin irin in nemi nearest makami in Illata dan iska, Sai dai ina fitowa dana cikin motar na yanke jiki na fadi a gurin. Na sake mikewa nayi taku uku zuwa hanyar gidan mu na sake faduwa ina jin kaina yana juyawa ganina yana gushewa. Sai da na huta sannan na kuma mikewa still not giving off, a haka na ja kafa har kofar gidan mu sannan na sake faduwa a gurin ina jin kaina kamar zai tsage. Na ga an haske ni da fitila, na saka hannuna na kare, naji muryar mai gadin gidan mu "Safiyya?" Sai ya koma da sauri ina jin sa yana magana "yallabai! Ga Safiyyan da naji ana nema" sai kuma gasu fara kokarin dagani "Fiyya? Are you okay? Lafiyar ki kuwa?" Na fara ture shi "karrrrr ka tabbba ni. 14 9 2 12:01 AM Dan isssska. Allah yaaaaa isaa na" and I realized cewa irin maganar yan shaye shaye nake yi. Sai naga ya sake ni ya tsaya yana kare min kallo, and he said the words "are you drunk?" A lokacin Daddy ya fito da sauri kamar zai fadi "Safiyya? Daga ina kike haka?" Nayi kokarin tafiya gurinsa cikin tangadi "daddddy" and I fall down again a kusa da kafafuwan sa. "She is drunk" Mustapha yayi concluding, Avi hakuri da wannan. *. *. *. *. * Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Thirty Nine : A Trap Kunga ji da neman indazaku samu kayan tsabtace muhallinku da kamsa sawa duk awuri daya to this is ur bustop El Wada's sun tanadar maku da komi d kuke bukata cikin Amin ci. Munda turarukan wuta irin su Sandaliya Arab Exclusive hawii White House Kajiji Special flasks Habeel florals Brown humra Classic VIP white humra Soulmate da sauransu Toilet cleaner Mopping mist Air fresheners Ceramic/ tile cleaner and more https://chat.whatsapp.com/ IHHSMB9AyPcEDUMpYkJh4a Muna marabada masu siyen daya ko sari. Not Edited A gigice Daddy ya fara kokarin daga ni. Na kama shi na mike amma saboda ba shi da karfi shima sai muka tafi kamar zamu fadi, Mustapha ya taho da niyyar taimaka mana sai na tura shi baya da hannuna. "kar ka taba ni na gaya maka" na fada cikin murya irin ta yan maye. Daddy ya ture shi shima yace "kar ka taba ta tunda bata so" Mustapha ya matsa gefe yana kallon mu sai na zagaye hannayena a wuyan Daddy na cusa fuskata a wuyansa na fara kuka, feeling safe at last. A haka ya tafi da ni ciki, muna ta tangadi tare kamar zamu fadi amma ya hana Mustapha kama ni saboda nace bana so, har muka shiga ciki sannan ya kwantar da ni akan kujera yana kallona fuskarsa cike da tashin hankali. Ya juya gurin Mustapha yace "call the doctor, da sauri" sannan ya juyo gurina "Safiyya?" Yace yana kallon cikin ido na "what happened to you?" Kafin inyi magana Mustapha da yake tsaye a gefe yace "wallahi Daddy wannan yarinyar a buge take, kalli idonta ka gani" Daddy ya mike a fusace "zaka je kayi abinda na aike ka kayi ne ko zaka cigaba da tsayawa a kaina kana gaya min maganar banza?" Mustapha ya juya da sauri ya fita, Daddy ya sake juyowa inda nake ya tsaya yana kallona, a hankali yace "inna lillahi wa inna ilaihir rajiun" na daga kai nima ina kallon sa sai naga kamar jujjuyawa yake yi ba'a tsaye yake a guri daya ba. Hatta bangon falon da kujerun gani nayi suna motsawa kamar wadanda suke yawo a cikin ruwa. Mustapha ya sake dawowa ya ajiye kayana na cikin mota a gabana "Daddy na ga motar ta a waje, kofar a bude, ga jakarta da wayarta nan ta bari a cikin motar, na shigo da motar ciki..... Daddy ya sake rufe shi da fada "I don't care about the car. Ka kira Dr din ko baka kira shi ba? And call the police as well" Mustapha yace "police kuma Daddy?" Daddy yace "yes, police" Na mayar da ido nana rufe, a take bacci ya sake daukata. Cikin baccin naji Daddy yana ta magana da karfi "I need the lab result now!" Na bude ido na kadan na ganshi a tsaye tare da doctor din da yake duba mu a Abuja, doctor din yace "kayi hakuri Alhaji ka zauna, ka ga ba lafiya ce da kai ba. Na dauki jininta ai gobe da safe zany duk tests din da suka dace a kai" Daddy ya girgiza kai "ba gobe da safe ba. Yanzu nake so kay running analysis din, in ba zaka yi ba in kira wani yayi" yace "za'a yi Alhaji. Zanje in bude lab din yanzu inyi, In zargin mu na cewa a buge take gaskiya ne zamu gani a jinin ta and then sai musan matakin da zamu dauka" Bayan ya fita Daddy ya lura da cewa na farka sai ya sake dawowa inda nake "Safiyya, wake up! Tashi ki gaya min abinda ya faru da ke? Daga ina kike? Me ya same ki? Tashi ki gaya min" nayi kokarin tashi amma naji na kasa, ko'ina na jiki na ciwo yake yi min amma kuma ciwon da yake cikin zuciyata yafi da jiki na damuna. Maimakon inyi magana sai na kama kuka, I should have told Daddy there and then what happened to me amma sai naji maganar tayi min nauyi da yawa inyi da mahaifina, and I missed my mother a ranar fiye da kowacce rana. Akwai maganganu da yawa da ya mace ba zata ¡ya yi da babanta ba sai dai da mahaifiyar ta, ni kuma bani da mahaifiyar, and the woman that is suppose to be my mother figure is the mother of the person da nake zargi da laifin rusa rayuwata, WhatsApp.com EL WADA'S GLOBAL VENTURES EM WhatsApp Group Invite 13 9 4 7:19 I had to switched off my phone saboda kiran da Muhammad yake ta yi min, and my heart broke for him dan nasan yana can cikin damuwa akan tafiya da nayi na barshi, yana kuma tunanin cewa ta tabbata yaudarar sa nake yi kuma karya nake yi masa da nace zan kawo shi gurin baba na. A falon muka kwana daga ni har Daddy, but I doubt shi yayi bacci ma throughout the night. Sanda na tashi da assuba naji allurar ya dan sake ni dan ina iya gani sosai sai dai ciwo da kaina yake yi sosai, sannan kuma jiki na gabaki daya yayi tsami. Na tashi da kyar na shiga dakina na hada ruwa nayi wanka and I cried kamar idanuna zasu fito lokacin da nake yin wankan, I felt like a used and discarded rag. I have heard about rape and read about some cases of rape online amma ban taba tunanin cewa haka feeling din yake ba, bakin cikin is undescribable in ba wanda ya shiga cikin matsalar ba, which bana yi wa kowa fatan ya shiga din, babu wa da zai fahimci abinda ake ji a cikin zuciya, Har lokacin kaina a toshe yake, dan haka ban samu nayi zurfin tunani akan komai ba ballantana in yanke wani hukunci mai ma'ana. Ina fitowa na saka riga a jikina kenan naji knocking a kofar dakina and muryar Mustapha, "Ki zo inji Daddy", Naji wani bacin rai ya tokare min kirjina, tsanar sa tana kara ninkuwa a cikin zuciyata. Ina saukowa naga Daddy a zaune. Na cigaba da tafiya a hankali ina dafa bango da kujera dan har lokacin kafafuwana karkarwa suke yi. Daddy ya bini da kallo, shi a tunanin sa har lokacin a cikin maye nake shi yasa nake irin wannan tafiyar. Na zauna a kasa ina kallon sa amma na kasa cewa komai. Ya sake tambaya ta "daga ina kike jiya da daddare? Me yasa muka yi ta kiran wayar ki ba kya dauka?" Na sunkuyar da kaina hawaye suna sake cigaba da bin fuskata. Na bude baki na wajen sau uku amma kalmomin sun kasa fitowa. Shin cewa zanyi Daddy I was raped yesterday ko kuma me zan ce? Na san dole zan fadi abinda ya faru ko dan a bi mini hakkina amma ba xan iya gayawa Daddy ba. Muna haka doctor din jiya ya shigo tare da Mustapha, ya zo ya gaishe da Daddy yana kallona sannan ya mikawa Daddy wata farar takarda, Daddy bai karba ba yace "tell me, Gaya min kawai" likitan ya dan yi gyaran murya yace "akwai percentage mai yawa na hard drug a cikin jinin ta" Daddy ya dafe fuskarsa da hannayensa biyu "innalillahi wa inna ilaihir rajiun" na dago kai na kalle shi, na jima banga tashin hankali a fuskar Daddy irin wannan ba. "Shaye shaye kike yi Safiyya?" Ya tambaye ni muryar sa cike da disappointment. Na kara karfin kuka na "Daddy wallahi ban sha komai ba, ka bari zanyi maka bayani" ya mike tsaye yayo kaina "yi min bayanib mana to inji, idan ba ki sha komai ba menene ya kawo hard drug cikin jinin ki?" Nayi shiru tare da rufe idona, maganar tana yin kuna a cikin zuciyata amma bakina ya kasa furtata. A lokacin ne naji abinda ban taba ji ba a rayuwata, saukar kyakkyawan mari akan kuncina, na bude idona a tsorace ina kallon Daddy, kafin in ankara wani marin ya kuma sauka wanda ya fi wancan karfi a daya kuncin. Karfin marin ya saka mayafin kaina ya kunce, sai ya kama gashina da hannunsa ya finciko ni fadi a tsakiyar falon "ba zaki gaya min gaskiya ba?", Doctor din da Mustapha suka taso da sauri suka rike shi, shima kansa neman faduwa yake yi. Na kwanta a inda ya jefar da ni ina kuka matsananci, Daddy bai taba duka na ba tunda aka haife ni duk kuwa da tarin laifuffuka na, amma yau gashi ya dake ni akan laifin da ban aikata ba, A lokacin naji sallamar wasu sun shigo gurin, na cigaba da kuka na ban tashi ba har suka zauna suna gaishe da Daddy amma bai amsa ba dan kamar magana ta dauke a bakin sa, a lokacin na fahimci police ne and I remembered Daddy mentioning police jiya cikin dare. Sai da Daddy ya gama mayar da numfashin sa sannan yace musu "ina so ku bincika min inda yarinyar nan take a jiya da dare. Ta dawo min gida a buge and something is telling me that there is something or someone behind that. Da akwai abinda ya faru wanda taki fada min" sai ya dauki passport size picture dina a aljihunsa ya mika musu "a M.D University take zaune a hostel. Ku fara binciken ku ta can. See if you can get their cctv ku ga sanda ta bar makarantar and if possible, with who" Nayi kokarin mikewa zaune ina jin wani sabon tsoron yana kamani. Muhammad ne yaje makaranta ya ajiye motarsa a can sannan muka fita tare a tawa. Kamar Daddy yaji abinda nake tunani sai yace da Mustapha "show them her car, su dauki hoton ta da details dinta", Sai da duk suka fita sannan ya dawo gurina yace min "in na tarar kina boye min wani mugun abu ko Safiyya, sai na babballaki". E3 Police din basu jima ba suka dawo suka yi reporting findings dinsu back to Daddy. Sunje MD din sunyi magana da security kuma sun basu access to cctv din gate din su, sannan kuma sunga fita ta daga makarantar "ba ita kadai ta fita ba, tare da wani suka fita a motar ta, but we couldn't get his face from the camera. Amma zamu cigaba da bincike, duk abinda muka samo zamu gaya maka". And Daddy almost lost his mind after that information "ku koma makarantar, press the security su baku more information, su gaya muku waye yake zuwa makaranta yana fitar min da yarinyar da na basu amana" sai kuma ya juyo kaina "waye shi? Waye a cikin motar ki jiya? Shi ya baki kwaya kika sha? Ina kuka je? Menene hadin ki da shi?" And by that time I knew gaskiya ta will mean nothing to Daddy. Duk ta inda na zaga ya na zagayo, Muhammad ne a ciki. *. *. *. Present days........ Muryar Mommy ce tayi cutting through tunani na. "Safiyya? Me kike yi ke kadai a zaune a cikin duhu?" Na juya na kalli side din da maganar take fitowa, side din kofar shigowa dakina. Sai a lokacin na lura da duhun da dakin yayi gani kuma a zaune a bakin gado. Ta lalubi switch ta kunna fitila dakin ya cika da haske. Na daga kai ina kallon ta. I have known her all my life, she have been and still is a mother figure in my life. Idan na d tana so na kamar yadda take son yayan ta tabbas nayi karya ita ma kuma in ta fadi haka tayi karya, saboda soyayyar uwa ga yayanta daban take, sai dai kuma a duk tsahon shekarun nan ni dai ba zance ga lokacin da ta cutar da ni bayyananniyar cutarwa ba, in ma tayi a boye to bani da tabbas except for sanda ta boyewa kowa including ni kaina maganar cikina, though she claimed that tayi ne to protect me from myself. 1 have never been a fan of her when growing up saboda tana da fada ni kuma ina da rashin jin magana. I have always been daddy's girl, akaina Daddy bai yarda da kowa ba including her. Wannan ya kawo musu sabani a tsakanin su sosai, in dai za'a ta ba ni sai Daddy yayi magana, ba ita ba ko waye, ita kuma komai kankantar abu idan nayi to bakin ta ba zai yi shiru ba ta dinga yi min fada kenan, But she does that to everyone, kawai dai ni dan na fi sauran fitina ne shi yasa nawa fadan ya fi na sauran yawa. A fahimta ta wannan sabanin da suke yawan samu a kaina shine silar rashin jituwar muni da Mustapha. In dai har zamu keve daga ni sai shi to sai ya ci zalina yace min munafuka, amma in a gaban mutane ne musamman a gaban Daddy to zsiyi6ta lallaba nine kamar wani babban wa na. Amma da sun juya bayan su zai dungume min kai ko yayi min wata muguntar, sometimes a gaban Safina, sai dai ko na kai kara in aka kira Safina shaida sai ta goyi bayansa ta ki fadar gaskiya. Ni kuma Mommy tayi ta min fada. A saboda irin haka har saida Daddy ya chanja min makaranta lokacin da muna primary school. Ya ware min makaranta ta daban driver na daban. Ai kuwa a kan hakan ma sai da suka yi rigima da Mommy tace zai raba kan mu saboda ina gaya masa karya. And then as we grow up, muguntar Mustapha sai ta chanja salo. As for Mommy, relationship din munya samu babbar baraka ne lokacin da Daddy ya ambata cewa nice nake da mallakin kusan duk abinda take tunanin ya mallaka, A lokacin ta chanja min kwata kwata daga ita har yayanta. Suka daina min magana suka daina shiga harkata except for twins da suke zagayewa ba tare da ta sani ba suyi min magana, suma in ta gansu sai randu ya baci. Babu inda ba ta je ba akan ayiwa Daddy magana ya rushe waccan maganar, tana ganin anyi mata ita da yaranta rashin adalci, duk wanda ta san Daddy yana jin maganar sa sai da taje ta kai kara gurinsa, sai da ta tabbatar magana dai haka take babu chanjawa sannan kuma ta hakura and I guess they moved to plan b, wanda a cikin sane ta jawo ni jikinta take nuna min soyayya da kulawa fiye da kowa a duniya, watakila a tunanin ta hakan zai saka in raba kudin da su ko kuma in daddy ya mutu in cigaba da kula da su. Sai kuma ga Mustapha of all people ya zagayo ya zo yace min wai yana so na yana son ya aure ni. Can you imagine the audacity? I rejected him outrightly. And few months after that I was raped and framed for shaye shaye, and the first thing Mommy did sanda maganar taje kunnen ta shine bada shawarar cewa ayi min aure, a aura min Mustapha. But that is a story for another day, Shin ta yaya ba zan ki taba? Ta yaya kuma ba zan zargi Mustapha akan abinda aka yi min ba? Amma kuma yanzu dan zargina akan Mukhtar ya tabbata hakan na nufin cewa they are innocent of that crime. Hakan na nufin maganar Daddy gaskiya ce da yace Mommy is not cruel. Ta karaso ta zauna a kusa da ni tare da rike hannuna a cikin nata tace "dole wanna rayuwar ta chanja Safiyya, ko so kike ki samu mental issue ne? Ta yaya zaki mayar da zama a cikin duhu tare da dogon tunani dabiar ki?" Na juya fuskata gefe tare da kokarin goge hawayen da yake jikin ta dan kar ta gani, and she said "and you have been crying too. Kukan nan ba zai kare ba ne ba wai?" Na goge hawayen tate da gyara murya ta sannan nace "nima na dauka na gama kukan. Ashe da saurana. Rayuwa keeps throwing things at me tun kafin in Zo duniya ma. I thought na kai karshe, I thought babu abinda zai sake bani mamaki ashe akwai saura na Mommy, ban kuma san menene rayuwa have in store for me nan gaba ba". Tayi ajiyar zuciya tace "nima haka, Ba zan iya ce miki menene zaki fuskanta nan gaba ba, amma kuma zan iya ce miki you are strong enough to face koma menene, because you are your mother's daughter, You are as hard as a stone". Sai na yi murmushi na mike na je na tsaya a gaban wani hoton mu ni da Ammi da yake dakin, a Oasis ne ta jefa ni sama ta mika hannu zata cafe ni, gabakidayan mu muna dariya. Na tsaya a gaban hoton sannan nace "no mommy, stone ana iya fasa shi with something as common as a hammer, I am harder than that. Ba kuma zan ce as hard as a steel ba, dan shima something as common as oxygen and water can destroy it" na juyo ina kallon ta nace "no Mommy, I am as hard and as precious as a diamond. Nothing, I mean nothing, can break a diamond, not even fire, except another diamond of cause" Tayi shiru tana kallona bata ce komai ba, sai na tambaye ta "saura kwana nawa biki na?" Ta yi mamakin tambayar amma sai ta amsa "kwana goma" nace "good. Very good “ Amma a raina na ga kwana goman kamar sunyi min yawa, I have waited nine months amma yanzu zuciya ta naji ba zata iya jiran ten days din ba kafin in kama wanda yay min wanna babban zaluncin. Shaidar kamannin ido ba zata ishe ni a court ko a gurin iyayen mu cewa Mukhtar ne yayi min wannan zaluncin ba, I need to request for a DNA test, and even that bana jin Mukhtar will just go willingly ya bada sample for the test, idan kuma na dauki sample din from him ba tare da saninsa ba zai iya denying yace it is not from him. Dan haka ina bukatar shaidar da zan tunkari iyayen mu ko hukuma da ita wadda zata saka su matsa masa ya bada sample openly for the test, and to get that dole in tare a gidan sa. Bayan na gama shirin kwanciya na kwanta, duk da nasan ba lallai in samu bacci mai kyau a wannan daren ba, sai ga kiran mukh6ya shigo wayata kamar yadda ya saba yi a yanzu kusan duk dare. Ganin sunan sa kawai da nayi sai naji wata irin tsanarsa tana cika dukkan ilahirin jikina. Wani irin rage that I have been bottling up for months yana cika zuciyata. Gani nake yi babu abinda zai bani satisfaction idan da ace kisa ba haramun bane ba irin in samu wuka mai kaifi in soka a makogwaron sa sannan in jawo ta kasa har cikin marar sa. Sai dai kuma wannan tunanin sai ya saka na fara tunanin anya tarewa ta a gidan sa shine mafita? Kar fa inzo in aikata abinda zai rusa dukkan kokarin da nake yi dan ganin na gyara rayuwata. Kiran ya katse wani ya sake shigowa sai na dauka, trying to force myself to play along zuwa sanda zan samu abinda nake nema. Ina dauka yace "maman boy, ko har kinyi bacci ne?" Sai na kara fahimtar wani abu da ban fahimta ba da, he have been asking for junior tunda na saka kafata a kasar nan. Pretending cewa saboda soyayyar da yake yi min ne ya saka yake son abinda na haifa ba ta hanyar aure ba. Nace "me kace?" Yayi sauri yace "cewa nayi amaryata" nace "ba haka kace ba, ka fadi abinda ka fara fada daga farko" yace "na fasa fadar wancan din ai, dan yanzu kin zama hukuma sai lallashi. Lallabawa nake yi har Allah ya dube ni ya cika min zuciyar ki da soyayya ta". Nayi kokarin bashi amsa ma ko da bakar magana ce amma naji zuciya ta ta toshe makogwaro na maganar ta ki fitowa. Ya cigaba "but seriously, you need to call them and ask them halin da yake ciki ko? You can't just leave him in the NICU, na san zuwa yanzu ya warware ya kamata ma ace sunyi discharging din sa. Ina zasu kai shi kenan?" Nayi gyaran murya nace "and how is that any of your concern? Idan ni ban damu da shi ba kai menene naka?" Yace "sorry.... .. Na san za'a vi haka dama. Relax, na daina maganar sa. So, ya yau din?" Na katse kiran tare da ajiye wayar. Me yasa wai tun farko ban fahimci inda mutumin nan ya dosa ba. But how could he did that to me? Why? Me nayi masa? Kawai sai na rungume pillow na fara rusa kuka ina jin ciwon abin yana dawo min sabo a zuciya ta. Washegari na tashi da kumburarriyar fuska da edgy mood, kowa a gidan sai da yayi receiving kason sa na bacin raina. Mustapha asked me me yake damuna and I told him to mind his business ko in bude file dinsa yanzu. Bai kara ce min komai ba. Hatta Daddy sai da ya tambaye ni abinda yake damuna sai nace masa bana jin dadi ne kawai. Sai kuma na nemi ayi postponing duk was pending businesses da suke bukatar attention dina till further notice. Naga Daddy ya damu da hakan amma a zuciya ta sai nace zai fahimta ne nan gaba, I then turned to Mommy na gaya mata she should count me out of every event na biki da ta shirya, suyi kayan su amma ni ba zanje ba because my mood was so messed up a lokacin na san in naje zan iya zagin mc ana tsakiya da biki Daddy ya kira ni har dakin sa ya tambaye ni menene yake damuna nace masa babu komai, he was worried ya ga kamar na koma yadda nake a watannin baya, but i assured him babu komai kawai ina bukatar time ne alone to process the whole marriage thing da yake doso ni. And he seemed to understand that. Har na tashi zan tafi sai ya kira sunana, na juyo ina kalion sa sai yace "kuna waya da Hajjo?" Na girgiza masa kai, yace "muna wata da Sufyan ina jin halin da yaron can yake ciki, ya gaya min an sallame shi daga asibiti, wannan weekend din ma zasu taho Nigeria gabakidaya. Kin sam za'a yi auren Abdul" na cigaba da shiru ban ce komai ba sai ya sake cewa "kina son ki ga hoton sa?" Nayi sauri na girgiza kai sannan na fita. A bangaren Mukhtar yayi ta neman waya ta baya samu, sai kawai ya dauko mota ya taho Kano. Ina daki na ina kan sallaya ina gayawa ubangiji matsaloli na kamar kullum sai gashi ya bude kofa ya shigo kan sa tsaye. Na daga kai na kalle shi, nan take zuciya ta ta fara aiyana min shi yana aikata min abinda aka yi min, na rufe idona kawai sai ga hawaye yana bin fuskata. Ya karaso da sauri ya tsuguna a gabana "innalillahi. ., Safiyya kuka fa kike yi? What happened? Nayi ta kiran ki bana samun ki? Me yaje damun ki?" And his concern broke my heart more, like how can you pretend to love and care for someone and then hurt them like that? What kind of a human being does that. Na goge hawaye na and I told him abinda dama na riga nayi planning gaya masa just to see how he would react and dan ya rabu dani ya daina damuna tun kafin inyi masa illa "they called me from the hospital, the boy is dead". And he reacted just like I expected. Saura kadan ya fadi daga tsugunnon da yayi, and his face shows it all, his reactions cleared dukkan sauran wasiwasi na, "What?" Yace cikin daga murya "what did you just said?" Ban maimaita ba na cigaba da kallon sa. "Yaushe suka gaya miki hakan? Ta yaya zasu fadi haka? Are they sure ya mutu? Ta yaya ya mutu?" Na cigaba da yin shiru ina kallon sa. Ya mike tsaye "we should go there, muje mu tabbatar, mu kai shi wani asibitin suyi double checking, How can he be dead now" Na gyara zamana ina kallon fuskar munafiki azzalumin da yayi min babban zalunci, already har na fara planning hanyoyin da zan rama, duk hanyoyin da nake planning din kuma babu mai kyau a cikin su. Calmly na kira sunan sa "Mukhtar" ya kalle ni bai amsa ba amma sai nace "he is dead. Ba kuma a kasar nan bane ba ballantana mu dauki mota mu tafi. He is dead, magana ta Wuce". Sai ya zauna akan kujera kamar wanda aka hankada, sannan ya saka hannu biyu ya dafe kansa, and I understood ya mugun dora ransa akan yaron da ko ganinsa bai taba yi ba. Sanda ya dago kai ya kalle ni idonsa ya kada yayi ja, yace "how can you let this happened? Tun farko me yasa zaki barshi shi kadai a wata kasar ke ki taho wata kasar? I am sure negligence ne ya kashe shi" a nutse na sake yi masa magana "me yasa ba zan taho nan in barshi a can ba? Kar ka manta he is a bastard. Ba shi da uba. I was gruesomely raped, a sanadiyyar haka na samu cikin sa, maybe ka manta ne. Maybe I need to remind you that he is not your son. Ko naka ne?" Yayi shiru yana kallona and then he blinked and brought back the mask of munafuncinsa, "haka ne, I am so sorry Safiyya. I shouldn't have shouted at you. Kiyi hakuri. What can I do to help?" Ya fada yana saukowa daga kan kujerar trying to hug me "na daga masa hannu tare da bata rai "Please no. You can help me by leaving ne alone, let me morn him in peace dan Allah. Kuma ina so duk wata hidima da ka shirya ta bikin nan ka cire nina ciki please, the goal is for me to marry you kuma an riga anyi, so kawai abinda nake jira shine akai ni gidan ka" Yayi ajjiyar zuciya tare da zama a kusa da ni. "Na fahimta. I am sorry Safiyya. Kiyi hakuri kinji?....…. Next year by now insha Allah da dan mu a hannun mu. And ina ganin ma wannan abin da ya faru is for the best for you and the boy. Allah ya sa mai ceton iyayensa ne" nace "Allah ya sa mai ceto nane. I am his only parent" yace "yes, right, haka ne. Ameen ya Rabbi. But still zan so ace kin barni na zauna tare da ke. I don't want to leave you alone a wannan yanayin" na girgiza kaina "I want to be alone" ya mike "okay .... Alright. Zan tafi, but sai gobe zan koma Abuja" ban ce masa komai ba sai ya juya, har ya kai bakin kofa na kira sunan sa, ya juyo nace "I will appreciate it idan maganar mutuwar yaron nan zata tsaya a tsakanin mu. Bana son mutane suyi ta min maganar" ya gyada kai cikin fahimta, ") understand, and thank you for letting me know", Yana fita na goge hawayen na sannan nace '"bakin munafuki Da sannu zaka girbi abinda ka shuka “ But na samu abinda nake so, peace and quite to make my plans, and I did made plans in batches, akwai plan A, akwai B akwai kuma C. Kuma a hankali duk na nema kuma na samu abubuwan da nake bukata to work the plans. Sai dai damuwa ta guda daya ita ce, the marks may have faded tun da wata tara kenan da faruwar lamarin, sannan kuma takamaimai ban san a ina zan duba a jikinsa inga marks din ba. Saboda ban san a ina na same shi ba. But my guess was cinyarsa ko kasan bayan sa. But koma a ina ne in dai yana nan sai na ganshi. Mommy taje Abuja suka gama jeren su, ta dawo tana ta labarin yadda gidan yayi kyau, harda kara kawo min wani list din na abubuwan da ta lura in aka saka zasu kara wa gidan kyau, na karba kawai na ajiye nace zan siya amma ni bani da niyyar yin ko da sati daya ne a gidan ballantana har in damu da kyan sa ko rashin kyansa. Ranar kamu suka zo ita da wasu cousins din Daddy suka gama hidimarsu suka fesa min turare suka tafi, Ranar da ta saka zata yi taron ta tazo, tayi taron ta a event center din da ta kama, and I have no idea wanne uzuri ta bawa mutanen da suka je gurin ha rashin zuwan amarya. Daga nan kuma sai aka fara shirin tafiya Abuja, twins suna ta tsokana ta wai zasu ga kukan rabuwa da Daddy amma ko kwalla banyi ba, shine dai kamar zaiyi kukan, ya zauna yayi ta min nasihar bin miji da hakuri da kiyaye dokokin Allah da sauran su amma ta kunnen hagu suke shiga duna fita ta kunnen dama. Sai da zan tafi sannan naje gabanss na durkusa na rike hannunsa nace "Daddy, for all the pain I have caused you, kayi hakuri, ka yafe min. Insha Allah, I will make everything okay, ko ba dan ni ba ko dan kai" ya dago ni jikinsa ya rungume ni yace cikin karyayyiyar murya, "na yafe miki Safiyya. Nima ki yafe min. You went through everything because of my wrong decisions, because of my weakness" sai na dago daga jikinsa nay kissing cheeks dinsa sannan na juya na tafi. A abuja muna zuwa muka tarar da Safina a gida, sai dana ganta sannan na fahimci abinda Mommy take fada, ta chanja gabakidaya and she looks somewhat depressed. Har da akwatin ta tace kwana biyu zata yi a gida wai mijinta baya nan yayi tafiya. Mommy ta fara fada "tun tafiyar da kika ce yayi har yanzu bai dawo ba?" Safina ta kalle ni na dauke kai sai tace "ya dawo, sake komawa yay" and I knew she was lying", O Yan bikin Abuja ne dai suka samu ganina tunda a gida aka yi, amma a daki na wuni sai dai duk me son ganin amarya ya hau ya ganni ko kwalli babu a ido na ya juya ya tafi. Sai da Hajiya tazo sannan na sauka gurinta saboda ba zata iva hawowa saman ba kuma tana da matsayi mai girma a gurina ba zan iya cewa ba zata ganni ba. Na sauka ita ma ta zauna tavi ta min nasiha da kuma bani labaran Ammie, a lokacin ne nayi kuka, shima ba kukan auren ba ne ba kukan kewar mahaifiya ta ne, ko yaya rayuwata zata kasance da ace tana da rai? Sai nayi kwanciya ta a jikin Hajiya anan falon har aka ce ga masu daukan amarya nan sun zo sannan Mommy ta kama ni muka koma sama. Haka tayi ta aikin shirya ni, ta shafa min wancan ta goga min wancan ta barbada min wancan. Ta zubo wani abu a kofi ta bani ta saka na shanye "kayan nan fa sai kina amfani da su na gaya miki, na fahimci ba son amfani kike yi da su ba. Kinga Safina har ta karar da nata yanzu zan bada order a kawo mata wasu, mazan ne sai da irin wadannan dabarun, ballantana nata mai shegen taurin kaj" sai na mike na fake da shiga bandaki just to get her to stop talking about mijin Safina in dai ba ina so wanna kai amaryar ya tarwatse ba. A haka aka dauke ni, na dauka gidan Mukhtar din za'a kaini sai naga an fara kaini gidan uncle Ahmad, sai a lokacin na tuna ko su Salima ban gani a gidan mu ba ballantana Umma. Aka zaunar da ni a gaban Umma Mommy ta fara jawabin bada amana ta "dama yar ki ce. Daga gida ta taho ta kuma zo gida. Ba dan ma Allah yayi haka ba ai da ke ce mai daukan ta ki kai ta dakin miji" sai Umma tace "'haka ne. Allah ya riga yayi babu yadda zamuyi. Jarabawa ce Allah yayi mana Allah bamu ikon cin ta baki daya" Mommy ta ce "wacce jarabawa kuma kike magana a kanta? Yarinya dai yarki ce kuma matar danki, kuma war jikokin ki nan gaba. In kin rungume ta kanki kika yiwa in kin watsar da ita ma haka. Abinda ma sani dai Safiyya bangon sikari ce duk wanda ya jingina da ita sai ya ji zaki, idan make ba ki jingina ba to an riga an jinginar miki kuma kin dandani zakin ta" da kyar aka lallaba Mommy tayi shiru, Umma tana ta cewa ita ba wani abu ta fada ba Mommyn ce tayi mata rashin fahimta. Ni dai kawai ina jin su. Ko Umma ta karbe ni ko kar ta karbe ni dama ba zama zanyi ba. Mutanen da suke gurin sai suka dauka rigima ce kawai su Mommy suke yi irin ta faccaloli. Daga nan sai gidan Mukhtar, gida ya cika da kamshi mai dadi da kuma sanyin ac. Aka wuce da ni bedroom din da suka ce C shine nawa akan zaunar dani masu nasiha nayi masu tsokana nayi ni dar ina lullube ina jin su, ina kuma Allah Allah su tafi su bani guri dan maganar Umma ta kara dada min tsanar auren da kuma dan nata baki daya. A haka har aka watse, saboda ban gayyaci kawayena ba ya sa Mommy tace Safina ta zauna da ni kar a barni ni kadai. Amma suna tafiya na bude fuskata ina kallonta tana danne danne a waya nace mata "zaki iya tafiya" ta mike tsaye ta dauki jakarta "dama ai ba zaman kaina nake ba, saka ni aka yi, kuma ina da gidan miji nima wanda yafi wannan ma" nayi murmushi "shi yasa naga kin bar gidan mijin naki kin taho gida, in har gidan mijin da dadi kiyi zamanki mana a can?" Ta yi murmushi sannan tace min "lallai rashin sani hausawa suka ce yafi dare duhu. Amma babu komai, nan gaba kadan zaki sani ai, zaki gane irin dadin da nake ji a gidan mijina. Ko kuma ince zaki gani da idonki" ta karasa maganar tana shafa marar ta, na kalli marar sannan na kalle ta ina jin zuciya ta tana kuna, tayi kamar zata tafi sai kuma ta sake juyo wa tace "fata na shine dan da zan haifa yayi kama da shi sak, at least kya rage zafi idan mun hadu kin ganshi. Before then, enjoy your own husband. Ina yi muku fatan zaman lafiya da zuri'a mai albarka". Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty: The Trap 2 Not edited please, Nayi kokarin danne zuciya ta da already dama a kusa take, amma sai hakan ya ki yiwuwa, I guess komai yana da limit dinsa, space din pretending hakuri ya kare a zuciya ta. Nace "babbar matsalar ki a rayuwa Safina shine kina da cutar karya, ke makaryaciya ce....." Ta girgiza kai tana murmushi "yes, I am a liar. But not this time Safiyya. Not about this. Idan baki yarda ba call him and ask him, that is idan zai daga kiranki. Dan ba ma shi da number dinki a yanzu, ko zaki gwada? In baki da number din in baki watakila ya gaya miki how crazy he is into me. Ohh na manta fake matar aure ce ko waya ba zaki iya yi da shi ba. Well good luck driving your own husband crazy" Na mike da sauri sai tayi sauri ta fita daga dakin, ban hakura ba na bita har falo sai tayi sauri tayi hanyar fita har tana hardewa kamar zata fadi. Na kira sunan ta '"Safina!" ta tsaya sannan ta juyo still da murmushi a fuskar ta, nace "ba zan tambaye ki abinda nayi miki a rayuwa kika yi min abinda kika yi min ba, ba kuma zanyi miki fatan ayi miki abinda kika yi min ba because that will be mercy for you, amma ki jira ni ina nan zuwa gare ki, da kaina zan dauki fansa a kanki ba zan jira karma ba, and when I am done with you, you will regret the ranar da kika dora idon ki a kansa". Na juya na koma dakin da na fito na koma na zauna a gurin da na tashi. Amma kuma zaman sai ya kasa yiwuwa. I kept rocking back and forth and kept fisting and unfisting my hands. Nasan da Dr Salma ES zata ganni a wannan yanayi da tabbas gado zata bani. Zafin da nake ji a zuciya ta ko makiyi na bana yi masa fatan ya ji irinsa. Na san cewa Safina makaryaciya ce tun muna yara, amma sai na rasa dalilin da yasa yau na bari kalamanta suka taba ni har haka, me yasa na kasa yarda cewa karya take yi yanzu? Me yasa nake tunanin gaskiya ta fada? Me yasa rayuwa zata zo min da haka? Me yasa nake fuskantar jarabawa ta kowanne bangare na rayuwata? Me yasa nake yiwa Muhammad irin wannan zazzafar soyayyar alhalin yana mijin yar'uwata ni kuma ina matar wani, Ban san mintuna ko awannin da na kwashe a haka ba sai ji nayi an bude kofar dakin an shigo, ban kalla ba amma na riga na san ko waye, and for the uncountable time naji ina fatan ace kisan kai halal ne da yau Mukhtar ba zai kwana a duniya ba. Ya karasa shigowa ya zagayo gabana ya tsaya. Ya sha kwalliya irin wacce ban taba ganin shi a cikin ta ba, fuskarsa dauke da farin cikin da ban taba gain shi a cikin sa ba. Ya ajiye ledojin hannunsa "amarya ta" na daga jajayen idanuna ina kallon, and I guess the eyes scared him dan lokaci daya naga murmushin fuskarsa ya bace, but he still tried to continue keeping his composure. Ya jawo kujera gaba na ya zauna yana cigaba da kallon fuskata. "Are you okay?" Ya tambaya cike da concern. Na girgiza kaina "no, I am not okay. I am not even close to being okay" na fada da murya mai cike da daci. Ya danyi gyaran murya, a fuskar sa ina ganin emotions da 02 yawa, a cikin su har da fear. "Me ya faru kuma? Talk to me. You can tell me anything" nace "anything?" Ya danyi karamin murmushi "yes, anything", Na gyara zamana na cire mayafin da yake jikina na ajiye nace "okay, Let me start from the most important thing. Kana son sanin abinda ya faru da ni? I was raped" na fada ina locking gaze with him, yayi saurin dauke idonsa daga cikin nawa sai na saka hannu na juyo da fuskar sa zuwa gare ni "anar 13th of last july, someone called me lokacin ina tare da Muhammad a restaurant yayi min karyar Daddy ba shi da lafiya, ya kira kansa da suna Mustapha kuma yayi faking muryar Mustapha, sanda na fito he almost suffocates me ta hanyar toshe min hanci da bakina sannan yayi min allura ta kwaya mai saka bacci, he kidnapped me and took me to......." Nayi shiru ina tunanin sannan nace "I don't even know where the hell he took me to, do you know why?". Ya hadiye yawn tashin hankali a makogwaronsa and I can already see streaks of gumi a goshinsa. "Why are you telling me this Safiyya? I don't want to know" ya fada yana kokarin tashi tsaye sai na kama hannun sa na rike gam sannan nima na mike "ohh but you have to know. You are my husband remember? Dole in gaya maka kuma dole ka sani. Ta yaya zamu fara aure da boye wa juna maganganu irin wadannan? That man took me somewhere that I do not know because ya daure min idanuna, ya daure min idanuna so tight that skull dina kamar min idanuna so tight that skull dina kamar zai tsage, he then raped me" ya kwace hannunsa tare da saka su ya rufe kunnuwan sa "na gaya miki bana son ji. I know you said something like that happened. But I do not want to know the details. Me yake damun ki ne wai?" Ya fada almost shouting but I didn't flinch. Na sake matsawa gabansa not minding banbancin girman jikin sa da nawa na cigaba da magana "he RAPED ME Mukhtar. And with that rape he took away everything da nake da shi a rayuwa ta, everything, including abubuwan da ban riga na samu ba ma. He killed me that day dan a yanzu babu abinda yayi saura a tare da ni sai bakin ciki da zafin zuciya da tunanin tarin abubuwan da na rasa" na fada hawaye yana zuba daga ido na kamar an bude fanfo. Cikin rawar murya Yace "am sorry Safiyya, am sorry that happened to you" nace "no you are not. Not yet. Ai ban gama baka labarin ba. Ya sake min wata allurar ai, he did not even care if jini na ba zai dauka ba ko kuma kwakwalwa ta zata buga , ko zan zama addict sanadiyyar hakan ko kuma na zan rasa raina ba ki daya, no, he did not care, ya sake yi min wata allurar, After he raped me sai ya dauko ni cikin maye ya dawo dani gidan mu ya yasar da ni a bakin hanya like a used and discarded rug, and wannan abin cost me my father's trust, har yau Daddy bai yarda cewa ba shaye shaye naje nayi ranar ba, kamar yadda bai yarda cewa ba zuna na aikata na samu ciki ba. Yes, rape din ya zama sanadiyyar da na samu ciki, sanadiyyar da na haifi da ba tare da aure ba, and that alone is a trauma beyond measures" ya rufe idonsa tare da jingina kansa a jikin bango, gumi yana bin goshinsa zuwa fuskarsa, sannan ya sake tambaya "why are you telling me this Safiyya?" Nace "kai ka tambaye ni. You asked me what happened to me shi yasa na ke baka labari" yace '"I did not wish to know all this, please stop telling me this" sai ya juya da sauri yayi hanyar fita daga dakin, na bishi nima da ssuri6naje ya sha gaban sa na tsaya muka cigaba da kallon juna, na tabbatar ya hango tarin tsanarsa da take cike a cikin idanuna kamar yadda ninma na hango tsoro da rashin gaskiya da suka cika nasa idon. Murya can kasa nace masa "but don't worry my husband. Ko waye ya aikata min hakan I promised him tun a lokacin da yake aikatawar that I will find him, and when I do, I will kill him. I will take his life just like he took mine". Na sauke idona kasa sannan na matsa na bashi hanya, bai kara cewa kala ba ya bude kofa ya fita. Na saka hannu na rufe kofar na murda key sannan na dawo na koma inda nake zaune na cigaba da zama idona akan frame dim da aka yiwa dakin ado da shi. I knew I messed up. I messed up big time, dan yanzu ya tabbatar na gano shi kuma zaiyi dukkan kokarin sa ya ga cewa ya kare kansa. But I didn't care because I let my anger out and I felt good. Na sauko daga kan gadon na jawo ledojin da ya shigo da su, kaji ne a leda manya manya masu zafi, daya kuma drinks ne masu tsadar gaske, sai dayar kuma fruits. Wato ya shirya celebrating wanna rana sosai. Na jawo kaza daya na bude sannan na dauko drink daya, ba zan iya planning the ways to get out of this mess cikin yunwa ba. Da safe tun kafin in bar kan sallaya ta naji tashin motar sa, and I wondered ina zai ie da sassafe? To ko guduwa zai yi ne? But I doubt idan zai gudu, not yanzu da yake ganin ya same ni, Wajan karfe goman safe sai ga Salima ta kawo mana abinci, Ta shigo har bed room muka zauna tana ta y min hira, a lokacin na fahimci kamar su basu san abinda ya faru da ni ba, basu san zancen ciki na ba, kamar iyayen ne kadai suka sani sai Mukhtar kuma. Tace "na dauka Umma zata so auren nan sosai saboda yadda take son ki, and she was in support before, yanzu sai naga duk tayi wani iri bata wani excitement, but she will get over it very soon tunda muna son ki mu da yaya" ta karasa tana winking at me, na kirkiri murmushi "and I love you too, kuma 1 appreciate the food dan ko kitchen din gidan nan ban san inda yake ba" ta mike tsaye tare da jan hannuna "tashi muje mu zagaya to, yaya bai zagaya da ke ba? And where is he by the way" nace "ya fita, something emergency. And thank you, kiyi zamanki kawai, zan zagaya later. Yanzu na gaji" she smiled ta koma ta zauna "amarya amarya, dole ki sha gajiya yarinya" nayi kamar ban fahimci abinda take nufi ba. Ban zagaya gidan ba kuma bani da niyyar zagayawa, dan da ace ban bar emotions dina sunyi getting the better of me ba da yanzu ina hanyar gidan iyayena. Bana jin har in bar gidan Mukhtar zan dora tukunya. Sai wajen zuhr ya dawo, sai a lokacin ni kuma na zauna ina cin abincin da Salima ta kawo min. Naji shigowar sa amma ban waiga ba sai ya zo ya zauna a kan kujera a kusa da ni, na juya na kalle shi and I saw a smile on his face "am sorry na fita na bar kike kadai, I had to go and see some of my friends up, dama jiya suna ta yi min mita ban shigo da su sunga amarya ba, ni kuma na san you will not like that" na cigaba da shan kunun madarar da yake cikin kofi a hannu na ba tare da na kalle shi ba. Ya jawo basket din abincin ya bude yace "Salima tace min dama zsta kawo mana abinci. She did well. Dama ko breakfast ban yi ba. Jiya ma ko dinner ban ci ba" na cigaba da yin shiru na har ya gama zuba abincin sa ya dawo ya zauna sosai yana ci sannan yace "Safiyya. I am glad we talked about that issue yesterday. I am glad you felt free to talk to me about that. Maganar ta fahimtar da ni abubuwa da yawa. It hurts me that you are hurting that way and there is nothing I can do about it. Da ace zan iya goge miki wannan bakin cikin da tabbas zan goge miki wanna memory din da tabbas na goge miki shi, but ba zan iya ba, abinda zan iya kawai shine a matsayi na na mijin ki a yanzu in tabbatar na baki dukkan kariyar da ta dace dake a yanzu, yadda babu wani abu da zai kuma samunki ko da wanda bai kama kafar wancan bane ba, I will protect you ko da kuwa a ce da rayuwa ta ne, I will make sure baki sake zubar da wani hawayen ba sai dai na farin ciki". Naii kunun da nake sha ya tsaya a wuyana ya ki wucewa, idan da akwai abu guda daya da na fahimta game da Mukhtar wanda duk tsahon shekarun da na sanshi ban fahimta ba sai yanzu shine he is a narcissist, he will gaslight you, sweet talk you out of blaming him and then hurt you physically and emotionally. Na ajiye cup din hannu na ina kallon sa nace "don't worry my husband, kar ka samu damuwa, I got emotional ne jiya shi yasa har nayi wadancan maganganun but maganar ta riga ta wuce" Na danyi murmushi "yesterday was suppose to be our first night and I ruined it. I am sorry yayi murmushi and I expected a hug a even a kiss but he didn't do any. I kept expecting physical touch from him amma still shiru har ya gama cin abincin ya tashi ya dauke ya dauke kayan gurin bai taba ko da hannu na ba. Da dare ya fita da kansa sai gashi ya dawo da abinci yace inji Umma, ya zauna ya gama cin kayansa kawai sai ya mike "good night darling, zan kwanta da wurj" yayi hamma "i am actually very exhausted, gobe kuma I have an appointment" ya sunkuyo yayi kissing cheek dina sannan ya shiga kofar da nake tunanin dakin sane a gurin. Na ajiye waya ta da take hannu na ina kallon kofar, lallai ma wanna mutumin. He is definitely planning something, amma me yake shiryawa? Mutumin da tun da aka daura auren nan baya iya cire dauke hannun sa daga jikina in dai muna tare shine yanzu zanyi kwana na biyu a gidan sa ba tare da ko hannu na ya rike ba? Washegari ma ya sake fita da safe, Salima suka dawo tare da Yaya (kanin Mukhtar mai sunan Daddy) suka kawo mana abinci, sannan ta kwashi kayan jiya ta tafi dasu tana ta sauri dan Yaya yace ba zai jira ta ba in dai ta dade tafiya zai yi ya bar ta. Basu jima da tafiya ba nayi bakuwa, the most unexpected bakuwa, Aunty Hajjo. Akayi knocking a tashi daga kwanciyar da nake akan kujera naie na bude half expecting Salima ce ta dawo, dan da Mukhtar ne yasan kofar a bude take shigowa kawai zai yi, Ina budewa muka hada ido, tayi murmushi ganin yadda fuskata ta cika da mamakin ganin ta. A rataye a gaban rigarta baby carrier ce, a cikin ta kuma akwai baby. Nayi iyakacin kokarin hana kaina kallon babyn. Nayi kokarin rungume ta sai ta jani ta gefe tace "zaki matse bawan Allah yana baccin sa" nayi dariya "sannu da zuwa Aunty, ya akayi kika san gidan nan?" Tace "Mommyn ki na kira ta bani address, munzo gari ai tun last weekend, naso shiga gidan ku ranar bikin ku but I didn't want to go with Junior" sai kuma ta fara kalle kalle "ke kadai ce dai ko?" Nayi murmushi tare da bata hanya ta shigo sosai "ni kadai ce" amma tana shigowa sai na rufe kofar na kuma murda key dan bana son Mukhtar yayi surprising dina yaji wani abun da ba zan so yaji ba. Ta zauna tare da ajiye katuwar baby bag din da take hannun ta sai kuma ta kunce baby carrier din ta sauko da shi ta kwantar dashi a kan kujera. "Sarkin son jiki, yanzu zaki ga ya tashi indai ya daina jin dumin mutum a jikin sa" na bishi da kallo, yayi girma sosai fiye da yadda na gani a hoto, ba zaka taba tsammanin preterm aka haife shi ba. And he looked more cute in real, ya turo harshen sa waje yana tsotsa kamar yadda yake yi ranar da na fara ganinsa. Na dauke idona daga kan sa sannan na gaishe ta. Ta amsa "ya taro? An sha biki. Allah ya sanya alkhairi. Naso zuwa ai to kuma Abdul yana busy shima ranar ballantana ya zauna min da Junior, and I didn't want to go with him saboda Sa'adatu" nayi shiru ban ce komai ba sai tace "zaki yi mamaki in na ce miki people actually believe cewa ni na haife shi" tavi dariya "har gida ake zuwa yi min barka, har da masu kawo min kayan barka" ta dauko wani set din toys daga cikin jakar gabanta tace "kinga wannan ma dazu kafin in fito wata makociyar mu anan garin ta shigo ta kawo masa, suna ta tsokanar Abdul wai sai da zaiyi aure sannan aka yi masa kan'" na sake yin shiru kaina a kasa ina wasa da yatsun hannuna, ta cigaba "amma na san Sa'adatu tana gain sa zata gane shi. Kuma ban sani ba ko kun gaya mata yana wajena. Tunda dai ta san sanda ta baro ni babu ciki a tare da ni kuma watannin sa wasu yi dai dai da haihuwar ki. Za kuma ta ¡ya gane kamanni" na sake kallon sa, he really looked like a mixture of me and Daddy, amma kuma in dai ba kana tunanin haka ba zaka kawai kalle shi ka fadi haka ba, sai dai in dama kana zargi. And I wondered if Mukhtar will recognize him. Kamar amsar tambaya ta sai naji an buga kofa, na mike ina jin faduwar gaba na je na leka naga shine, amma kuma ai ba zai kawo komai ba dan ya ganni da bakuwa mai jariri, right? Na bude kofar na bashi hanya ya shigo "you locked the door? Ke da waye?" And he saw Aunty Hajjo a zaune. Nace "matar abokin Daddy ce" a fuskarsa naga alamar bai san ta ba. Ya gaishe ta ta amsa sai ya wuce zuwa dakin sa. Ina zama tace min "me zaki zauna kiyi, tashi ki bishi. Bara in hada wa yaron nan madara naga yana kokarin tashi" ta dan lakuce masa fuska "a cici" na wuce ta na shiga inda Mukhtar ya shiga, wani dan corridor ne da kofofi guda biyu, na bude daya sai naga falo ne kuma yana da kofa daga waje, na rufe na bude daya kofar sai na ganshi a ciki yana kokarin cire rigarsa, na tsaya a bakin kofar muna kallon juna, I half expected him to put it back on amma sai naga ya karasa cire wa yana kallo na expression din sa unreadable. Ya ajiye ta akan gado sannan ya fara kokarin cire dogon wandon jikinsa, zuciya ta ta fara dukan tara tara, ina jin toro dan ban tana ganin babban namiji yana cire kaya a gaba na kuma daga ni sai shi a daki ba, sannan kuma there was anticipation of maybe zan ga abinda nake nema, abinda nazo gidan dan in gani. Ya cire wandon ya ajiye shi shima, ya zama daga shi sai singlet da gajeren wando. Na fara bin jikin sa da kallo a hankali tun daga kan kafadar sa zuwa rabin cinyoyin sa da suke a waje zuwa kafafuwansa. Sai da na kai kasa sannan na sake dawowa sama. A lokacin muka hada ido and he was smiling, na dauke kaina daga fuskarsa na kalli gefe, yayi dariya "to ya? Are you satisfied with abinda kika gani or should I show you more" nayi gyaran murya "yau ma ka sake fita da wuri baka ci abinci ba, ina kaje?" Na fada a kokari na na chanja topic din, ya fara tahowa inda nake, sai naga ya kara yin girma, almost scaring me amma na rike stance dina naki motsawa har ya karaso inda nake "will you like to see more?" Ya fada da daskararriyar murya, na kalle shi cikin ido nace "oh yes, I can't wait. But ina da bakuwa a falo. So zany reserving show din for another time" sai nayi sauri na bude kofa zan fita sai ya saka hannu ya mayar da ita ya rufe, na juyo muka sake hada ido and the look in his eyes scared me. "What if I said now, your bakuwa can wait" nayi kokarin tura shi baya amma ko motsi bai yi ba "no, she cannot wait, Sauri take yi, tafiya zata y" yayi kokarin hada bakin sa da nawa sai na zame ta kasan hannunsa na koma cikin dakin, Ya juyo yana kallona tare da jingina bayansa da jikin kofar yana murmushi "okay…..okay .. na yarda, let reserve the show for another time. But, in kina son fita daga dakin nan you have to kiss me first, sai in baki hanya ki fita, I promise, just a kiss shikenan" na girgiza kaina. I planned on kissing him, on doing anything to get to see what I want to see, but not here, not in his room, not when he is 10x stronger than me. Wayata da take hannuna tayi kara number din Mommy, nace ina kallon wayar "kaga tana kira na, har ta gaji da jira, dama ta ce min tafiya zata yi" sai kuma yayi ajjiyar zuciya ya matsa daga bakin kofar ya koma ya zauna a bakin gado "shikenan, you can go. Babu dadi a bar bakuwa tana jira" na wuce shi nayi hanyar fita, half expecting zai tashi ya kama ni because the lost I saw in his eyes ba kadan ba ce ba. And something in my mind told me ba dan bakuwa ya bar ni na fito ba. Ina komawa falo na tarar da ita har gama feeding dinsa ya saka shi a kafadar ta, na wuce kitchen na hado mata anything da na san zata so na kawo mata, tayi min godiya sannan tace "ba zama zanyi ba ma, naga mijin ki ya dawo, But I was hoping zan bar miki shi a gurinki inje unguwa in dawo" ta fada tana murmushi, sai na fahimci ba wai dan zata je unguwar ba ne ba tana so ne kawai ta bani dama inga Junior sosai, amma sai naji bana son hakan especially with Mukhtar a gidan. Amma kuma ina so .... Na girgiza kaina "I cannot do it, kar inje inyi masa wani abu ba dai dai ba. I have never been around babies. What if in na dauke shi ya zame ya fadi? Ko in ya fara kuka ya zanyi masa? Me zan bashi in yaji yunwa?" Tayi murmushi ganin yadda duk na rikice "you will do just fine. I want you to be with him ko da for an hour ne or two, yanzu zan dawo. Akwai wata friend dina Zainab Aliyu, tun secondary school muke tare da ita, kwanan baya tayi bikin yayanta har guda biyu ban samu zuwa ba shine yanzu xan leka inyi mata Allah ya sanya alkhairi. Ba dadewa zanyi ba. Zan kuma nuna miki yadda zaki yi komai" na gyada kai ina jin excitement, I have never been around babies kamar yadda na gaya mata, tun ina five years aka haifi twins dan haka ba zan iya tuna komai akan jarirantakar su ba, daga kan su kuma babu inda aka sake haihuwa a cikin gidajen da nake zama, Gidan uncle Ahmad ma Salim da Salima ne auta, shekara daya kuma na basu, Ta miko min shi, yadda zan dauke shima sai da ta nuna min and he felt heavier than I expected. Ya fara mutsu mutsu na zaro ido "zai fadi, Aunty ki karbe shi zai fadi" tayi dariya sosai amma sai naga na gyara rikon sa da kaina ba tare da ta gyara min ba. Sai ta nuna min yadda zan hada masa madara idan ya ji yunwa da kuma lokacin da ya kamata ace aji yunwar. Ta nuna mun yadda zanyi wearing baby carrier din ajikina in kuma saka shi a ciki idan zaiyi bacci, ta nuna min yadda zan chanja masa diaper da kuma favorite toy din sa. Tana tafiya na kwashe shi da kayan sa na tafi da shi guest's room dina. Na rufe kofa sannan na kwantar da shi a kan gadon dakin ina kallon sa, ya kura min ido yana kallona, maybe yaga fuskar da bai sani ba. Na shafa hancinsa da dan yatsa na nace "hey you, how have you been?" Sai kawai naga ya kai wa yatsan na wa wawura, ya kama shi da hannu biyu sannan ya ja shi zuwa bakin sa ya kama tsotsa yana kallona, na bude ido "da gaske ne kenan abinda ake gaya min akan ka? Da gaske ne kenan kai acici ne" sai kuma na fara jin tsoro, what if hannun nawa akwai germs a jiki, what if ya dauki cuta a jikin hannun nawa. Nayi kokarin zare dan yatsa na daga bakin sa da hannun sa but he held it tighter da karfin da ban dauka yana da irin sa ba. Nace "hey, me aunty Hajjo taje baka ne kake da karfi haka. Give me back my finger" ban ankara ba sai ji nayi ya gatsa min cizo, nayi sauri na zare hannuna pretending kamar naji zafi "me nayi maka? Never bit the hand that feeds you" sai naga yayi dariya, dariya da bakin da babu hakori ko daya and I smiled, thanking Aunty Hajjo for giving me this moment. Anan muka yi bacci tare ni da shi. Ina tashi naji Mukhtar ya sake fita. Na dauko waya ta nayi order abinci online sannan naje nayi sallah kafin in idar har ya tashi ya fara rigima, a rikice na hada masa madara na bashi sannan na chanja masa diaper da kaya, I then took some pictures of him, of him and me and then my heart breaks sanda naji sallamar aunty Hajjo. I cursed the man da ya saka ba zan zauna da da na ba. I cursed my society Kafin su tafi mukayi maganar bikin Abdul, ta sake tambaya ta "kin gaya wa Sa'adatu maganar yaron nan?" Na girgiza kai, har yau na kasa gayawa Mommy saboda ina son Junior sosai and I planned on protecting him with everything in me, ita kuma Mommy har yanzu ban san matsayin da zan ajiye ta ba. A karshe sai nayi deciding in barwa destiny tayi deciding for me. Nace mata "ban gaya mata inda yake ba, don't tell her, amma in ta gano da kanta shikenan". Abinda ya faru da rana ya saka nayi tunanin something will happened tsakani na da Mukhtar da dare but it did not. Ya dawo gida da dare har da balangun sa cike a leda ya zauna ya baje a falo yana tayi min hirar friends dinsa and how they reacted to him getting married babu dinner. Ya gama ya tashi ya karkade rigarsa yace "good night dearest, kiyi bacci mai dadi" na mike tsaye ina jin raina yana baci, bana son sake spending another night breathing under the same roof with him, nace "what about the show? You promised me a show tonight" yay murmushi "don't worry sweetheart, zaki samu show dinki but not tonight, da mace miki nayi another time, bance miki tonight ba" na matsa kusa da shi tare da saka hannu ina kokarin balle buttons din rigarsa, "why not? What are you waiting for?" Ya ture hannuna '"'I promised to take care of you didn't I? And yanzu baki da lafiya, your stitches are still raw and you are not emotionally ready for this" na kama hannun sa na fara kokarin jan sa ta karfi "but I am ready, I am more than ready. Kazo muje dakina and I will show you how ready I am" ja daya yayi ya zare hannun sa daga cikin nawa still yana murmushi yace "good night sweetheart", Washegari na sake yin wata bakuwar, Mommy, tazo zata yi min sallama zasu koma Kano. Tayi ta tambaya ta ko ina da problem ko kuma da akwai abinda nake so, "you look drained....... Kamar ba amarya ba. Kina samu kiyi bacci kuwa sosai ki huta? Kina cin abinci ki koshi?" Nayi dariya, tayi ajjiyar zuciya "to ni dai aurar da yaya bai karbe ni ba. Ni dai na san in akayi aure a zamanin mu daga amaryar har angon kana ganin zu zaka gane, har kyalli zaka ga suna yi saboda samun nutsuwar zuciya, amma ke ji bi idonki yadda yayi rami, ita kuma waccan gata can kamar na bawa mayu ajjiyar ta suna lasar ta kullum" sai ta yi shiru, and I knew I was into trouble dan nasan labarin Safina zata bani, na fara tunanin abinda zan fada in chanja topic amma kafin in fada already ta fara "ko da yake na gane lafiya ce bata da ita kwana biyu, ga mijin baya nan. Nace taje asibiti kuma taki zuwa. Ina tunanin kamar ciki ne da ita. Na dai tura mata Dr Abbas ya duba ta, nace yayi mata pt, tunda su ba zasu kula min da yar ba ni zan kula da abata" nayi shiru yayin da ni kuma na rufe ido na, trying so hard not to think about maganar da take yi, ta cigaba "na daukar mata dai yan aiki biyu su sannan na dauko mata wata yar uwarta daga Katsina ta taya ta zama, at least ta ringa samun wadda zata ke magana da ita. Yanzu kawai damuwata rashin mota da bata da ita, ga motocinsa nan a gidan ya ajiye amma wai bai bar mata key din ko daya ba, shine nace. ." Na juyo tana kalion na, and 1 already know abinda zata tambaya sai dai yanayin fuskata kadai ya tabbatar mata ba zanyi abinda take so din ba. Ta chanja layi "shikenan kawai. Zan bata tawa motar ni ai ba zan rasa motar hawa ba" still bance komai ba sai kuma ta sake cewa "yauwa Safiyya, nay magana da Safina kema kuma yanzu zanyi magana da ke. Na rasa me yake damun ku. You two don't act like sisters, farko nasan it was because of what happened to you, you grew distant from every one, amma yanzu na ga kamar kin dawo dai dai, kamar kin shirya da kowa amma banda Safina why?" Nace "babu komai Mommy, kawai dai dan bama tare ne" tace "to ai yanzu kuna tare, ga ku Allah ya kawo ku aure gari daya, ku daure kuyi zumunci dan Allah. Be each other's keepers. Ku ringa haka wa kuna binne wa tare, duk wacce take da problem ku hadu ku samo solution ba tare da mu iyayen ku mun sani ba ma. I want you to be kamar yadida muke ni da Safiya in our days. Kinji Safiyya?" Na gyada kai "okay Mommy" ta sake cewa "a gaya mata next weekend tazo nan ku wuni tare, in kin samu dama ke ma sai ki je ki wunar mata" na sake amsa mata. Ranar da dare na shirya yin abinda banyi niyyar yi ba a da. Sai da na tabbatar da komai nawa yana in place sannan na shirya with only a pant and bra na dora rigar da take da ita da babu duk daya na zauna jiran Mukhtar. Bai dawo ba sai dare sosai, Ina jin shigowar sa na tashi na bude kofar dakin da nake ciki na tsaya a bakin kofa. Ya bude kofa sannan ya rufe, na lura a hankali yake yi a tunaninsa nayi bacci. Yana juyo wa muka hada ido and he dropped his car keys ya saki baki yana kallona, Na gyara tsayuwata feeling very awkward nace "come to bed, husband". Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty One: "Goodbye Husband" Al'ummar jihar Jigawa da kewayenta har ma da jihohin kusa . Haifa foods and pastries ta zo muku da kayan maqulashe kala kala irin su yogo fura wanda babu kamar sa ga dadi ga qoshi ga gardin shi badaganan©️ wani abun saima ka dandana. Ga irin su milk cake (sunan wani abu wai farfesun madara) wanda babu kamar shi ga sauqi ga dadi, cocunut milk wanda har getare babu kamar shi da kuma uwa uba Yogo fruits wanda ze gara muku Ify. Zaku sami kayan HAIFA har kofan gidajenku in kuna so ga komai na HAIFA a farashi mai sauki yake ku garzaya ku dandana kayan dadin Haifa 0812 536 8737 https://www.instagram.com haifa_foods_and_pastries iigsh=NHYyN2k1eTlhenBt&utm_ source=gr *. *. *. *. Ina kallon sanda ya hadiye wani mugun yawu sannan ya fara girgiza kansa, "What are you doing Fiyya. Na gaya miki baki da lafiya. I don't want to hurt you" na fara cat walking zuwa inda yake tsaye "really? Even if that's the case then we will be careful. I know you will not hurt me. I trust you" na tsaya half way from him, studying yadda yake bina da kallon, yadda idanunsa suke juyewa, and I hated myself for doing that. But I have already started dan haka sai na karasa. Na saka hannu na sauke kafadar rigar jikina guda daya, it slid down my arms and exposed more of my skin, he started taking steps toward me and I gave him a look da nake tunanin is seductive and turned around, signalling him with my hand to follow me sannan cikin tafiyar da na tabbatar ba zai iya resisting ba na koma dakin da na fito daga ciki. Ina shiga na kalli gadon da sauri making sure cewa the handcuffs I kept locked at each side of the bed suna nan but completely hidden sai dai in kasan da zaman su, na san cewa wasa nake da wuta kuma probability is very high that wutar zata kona ni but I was ready to get burnt in dai zan samu abinda nake bukata, Sai dai kuma zuciya ta da gangar jiki na cike suke da tsoro, kayan ciki na har karkarwa suke yi. Naji shigowar sa nayi sauri na juya dan bana so in dauke ido na daga gare shi even for a second. Ya tsaya a bakin kofa yana cigaba da kallo na, and akwai wani murmushi da na kasa fahimta a lips din shi. Ya karasa shigowa "you are seducing me" ya fada directly, but daga muryarsa na san I got him right where I wanted him. Nayi kokarin yin magana but abinda kawai yake kwakwalwa ta was that night, the pain, the darkness, the fear, the........ "Are you sure you know what you are getting yourself into?" Ya sake fada, bitting his lips. Nayi taku biyu zuwa gareshi "is it a crime idan mata tayi seducing mijinta? I am not made of stone and I have a husband. Besides, you promised me a show ranar nan, I want to see the complete show". Ya karaso gaba na, looking down at me "you want a show? You really want a show? You will have a show" ya fada muryar sa a cikin kirjin sa sannan ya dora hannayensa akan kafaduna tare da kokarin jawo ni closer to him at the same time trying to kiss me. All | wanted a lokacin was to scream on top of my voice, to scream out all my anger and hatred for him, to stab him in one place or two, amma instead sai na zame daga gare shi na koma kan gado na zauna, close to the spot da na makala one of my handcuffs. Ya juyo yana kallo na, sai kuma ya tafi gurin light switch ya dora hannunsa akai da niyya kashewa. Na mike da sauri, "Please, no, I hate the dark. It scares me" and I meant that har cikin raina. Ya juyo yana kallona and I saw him shakes his head sannan yace "no!" Na kara matsowa "please leave the light on" sai ya matsa daga kusa da ni ya sake cewa "no" na tsaya kawai ina kallon sa, na fahimci guduwa yake shirin sake yi ya juya min baya da sauri trying to stop looking at me "no, you are sick, and we shouldn't do this sai kin warke" yana gama fadar haka yayi hanyar fita da sauri. Na bishi nima da sauri na kama hannun sa da hannu daya sannan na juyo da fuskar sa da daya hannun "i am not sick, come, will show you that I am fine" and then he smiled at me, a smile that confirmed all my suspicious "not tonight, sweetheart" sannan ya juya ya fita. Na koma da baya har sai da kafafuwa na suka ta ba gadon dakin sannan na zauna akan sa. Yanzu shikenan? I have belittled myself for nothing? Amma kuma sai naji wani relief a wani bangaren zuciya ta, I wasn't sure my plan A will work and wannan abinda ya faru ya tabbatar min da cewa plan A is off. Dama na shirya plan A din ne saboda akwai remnants of shakku a zuciya ta na cewa shi ya aikata min wancan laifin. Bana son in dauki alhakin sa idan shi innocent ne and I risked everything to avoid that. Amma yanzu, the way he rejected me bayan na san babu abinda yake so irin to have me, ya tabbatar min da cewa shi din dai shine. Ba fariya ba, yadda Allah ya tsara jikina, dan ma dai har yanzu ban dawo yadda nake ba, ba Mukhtar da ya jima yana lusting for me ba, bana jin akwai namijin da zan bude masa jikina kamar yadda na bude wa Mukhtar yau, sannan mu shiga daki daga ni sai shi, sannan ga igiyar aure uku a tsakanin mu, kuma ace yayi rejecting dina yayi tafiyarsa. Wannan ya kara tabbatar min da abu uku, na farko Mukhtar ne yayi raping dina, na biyu kuma ya san ina zargin shi, na uku and the most important thing shine the scar is there, A yadda na bashi labarin daren da akayi raping dina in details ya tabbatar masa da cewa ina cikin hayyacina sanda na ji masa ciwo, and the way that I tried seducing him tonight bayan halin ko in kula da nake nuna masa kafin in tare ya tabbatar masa da cewa shaida nake nema a kansa, kuma wannan scar din ita ce shaida. Wannan realization din kuma sai yay unblocking another fear in me, he will now try to get rid of the scar ta kowanne hali. Tunda a ganin sa ita kadai ce shaidar da zata tabbatar min da kuma duniya cewa shine. Musamman tunda yana tunanin Junior ya mutu. And that was where I had upper hands in the matter, na kuma gode Allah da yasa nayi wancan tunanin dan in da yasan Junior yana raye kuma ya san ina zargin sa zai iya kokarin ma kawar da ni daga duniya to cover his crime. Wannan daren shine ya kawo karshen plan A dina. My plan A was to seduce him to my bed, handcuff both his hands idan na dauke masa hankali da jikina, and then check his body for the scars. It was risky but worth a trial considering bani da tabbas din shine dan haka bana son cutar da shi. Yanzu kuma it is going to be an eye for an eye. Dan yanzu zamu shiga plan B. Sai dai kuma daga alama shima Mukhtar ya chanja takunsa gabaki daya. Dan ganin shi ma daga ranar gagara ta yayi. Da asuba yake fita, sai cikin dare kuma yake dawowa, wani lokacin ma in ya tashi dawowa ta can daya kofar falonsa yake shiga zuwa dakinsa sannan in zai fita ma ya fita ta can. Mun koma kamar mage da bera a cikin gidan auren mu. And that frustrate me more than anything. Kamar yadda nayi alkawari ba zan yi girki a gidan Mukhtar ba, ban taba dafa ko da noddles ba, order abinci nake yi kuma a kawo min har gida. Shima kuma bai taba tambaya ta abinci ba, ban san kuma inda yake zuwa ya ci ba. And I didn't care. Bai taba kawo abokansa gidan ba, nima kuma ban gayyaci kawayena ba duk kuwa da korafin da suka ringa yi min a waya cewa anyi bikina amma ban gayyace su ba kuma gidan nawa ma ban gayyace su ba, I told them suyi hakuri abin ne yazo min lokaci daya amma na yi musu alkawarin shirya musu walima wata rana. Amma na fada musu hakan ne dan su rabu da ni inyi concentrating akan abinda yake gaba na. Sati biyu da biki na aka yi na Abdul. Tun kafin bikin na kira shi a waya nayi masa murna tare da lallaba shi da kyar ya turo min account details dinsa and I sent him heavy da sai da uncle Sufyan da kansa ya kira Daddy and Daddy said babu ruwansa ni nayi niyya kuma tsakanin mu da Abdul ne. Lokacin bikin Abdul Mommy tazo gari, dama munyi waya da ita tace min in shirya zata zo muje gidan bikin tare ni da ita da Safina, and I wasn't looking forward to that. Nayi ta neman hanyar da zan zame in fasa zuwa na rasa kuma gashi ina son zuwa din ko dan Aunty Hajjo, na san zata ji dadi sosai idan naje. But I was in no mood to neither meet nor talk to Safina. Sai dai cikin ikon Allah ranar da Mommy ta zo gari take gaya min Safina ba zata samu damar zuwa ba, bata da lafiya, "gashi shi kuma mijin nata har yanzu bai dawo ba, ina tunanin da ita zan koma Kano gaskiya, gwara in san a gabana take, ko kuma in je gidan iyayen nasa inji me zasu ce, amma wannan ai ba aure ba ne ba" ban ce komai ba kuma banyi niyyar cewa komai ba, sai kuma tace "ya kamata dai kije ki duba ta" nace "insha Allah". Amma sai naji dadin cewa ba zan hadu da Safina ba, Ranar yini Mommy tazo ta dauke ni muka je tare. I kept thinking ko zamu ga Junior? Ko zata gane shi? Amma da yake a event center akayi bikin I guess Aunty Hajjo bata tafi da shi ba dan duk baza ido na ban ganshi ba. Washegari da dare muka sake zuwa dinner. Aunty Hajjo taji dadin ganin mu sosai kuma ta karrama mu sosai, naje har gurin ango da amarya na taya su murna and they looked so happy and so in love with each other. Abdul yayi introducing dina a grin amaryarsa muka gaisa sosai, yana tsokana ta wai ina ango na. Sai ganin su naji ya fama min wani ciwo a zuciya ta da nake ta ajjiye da shi, and as I sat down looking at them I thought about him, ko ina yake? Ko me yake ciki? And I so much wanted to unblock his phone number and call him, maybe inyi pretending kamar babu abinda ya faru and say '"tsokanar ka fa nake yi Yaya Muhammad. It was all a prank. I miss you so much", I remembered the sound of his voice over the phone, the deepness of it and how it has always reach deep into my heart "hey Piya, you have no idea how much I miss you" na sunkuyar da ido na kasa ina jin hawaye yana taruwa a idona, a hankali nace "I miss you too Yaya Muhammad". A lokacin ne naji Mommy tana taba ni "Kinga mother in law din Safina, Ashe ta san su Sufyan" nayi sauri na dago kai and I saw her tana tafiya zata zauna. Ban taba ganin ta ba amma na tabbatar ko da kuwa Mommy bata nuna min ita ba zan iya gane ta idan na ganta. Kana ganin ta indai kasan Muhammad to zaka san cewa ita ta haife shi. Mommy ta ja hannuna "zo muje ku gaisa da ita" na zame hannu na tare da langwabe kai "Mommy please" tace "ke fa matsalar ki kenan ba kya son mutane, ai sai kiyi ta zama" ta tafi ta barni. Nayi ajiyar zuciya na cigaba da kallon Mama da ga nesa, naki zuwa ne saboda ina jin toro, ban sani ba ko ta taba ganin hotona a wayar Muhammad ko something like that, ina tsoron kar ta gane ni, duk da dai na san karin maganar hausawa da suke cewa idan kere na yawo zabo na yawo watarana dole za'a hadu. Wasa wasa dai sai naga Mommy ta samu kujera a can ta zauna sun cigaba da hira. Ni dai ina zaune a guri daya har aka gama sannan Mommy ta zo muka tafi. Tun kafin mu fita na san cewa I was in for hirar Safina da mijinta har muje gida, ai kuwa dai muna shiga mota ta fara "mutanen nan suna da son kansu wallahi, kinji wai basu san Safina babu lafiya ba, wai bata gaya musu ba shima bai gaya musu ba, Amma dai munyi magana tace zata je gidan ta dauke ta ta mayar da ita can gabanta su zauna tare kafin mijin ya dawo. Ai ce mata kawai nayi tafiya zanyi da Safina Kano inyi jinyar ta a can" naji kamar in toshe kunnena irin yadda nake mata in bana son jin maganar da take yi sai kuma na fasa, tunda na mayar da zargina kan Mukhtar a fara sassautowa akan Mommy. Sai kuma tayi ajjiyar zuciya tace "ni tausayi take bani yarinyar nan, Allah ya sassauta mata wanna lamarin. Ko babu komai iyayensa masu kirki ne". Ranar daurin aure ma muka sake komawa gidan Aunty Hajjo, ranar ni na fara fita a motata naje na dauki Mommy sannan muka wuce, muna yin packing na dauko envelope din dana taho da ita da kudi masu kauri a ciki na mika wa mommy nace "gashi Mommy ko zaki bawa Aunty gudummawa" ai kam taji dadin haka sosai "kai amma kin kyauta Safiyya, dama ina ta tunanin abinda zan bata na rasa" nayi murmushi kawai na fita. Ranar babu mutane sosai tunda daurin aure ne, sai yan uwansu na jiki sai kuma few close friends kamar mu. Muka zauna a falo Mommy ta samu wata yar uwar Aunty Hajjo itama mai surutu suna ta zance ni kuma na koma gefe ina ta rubuta wani sabon plan da nake shiryawa akan maganar reopening Oasis da nake son yi as soon as I get rid of Mukhtar. Muna nan sai ga wata yarinya ta shigo falon da Junior a hannunta, tazo ta zauna opposite din su mommy ta na bashi madara shi kuma yana ta rigima yaki sha sai dawo da ita yake yi. Na ajiye waya ta akan cinyata ina kallon su. Kanwar Aunty Hajjo ta juya gurin su itama tace "ke Husna yaron nan fa ya koshi, daga alama bacci yake ji ki goya shi mana" wadda aka kira da Husna ta kwabe fuska kamar zata yi kuka tace "na goya shin fa yaki yin baccin wallahi. Wannan yaron rigimamme ne" Mommy ta juya tana kallon su ita ma sai tace "ki kaiwa maman sa shi mana to, maybe goyon ne baki iya ba" yarinyar tace "to ai maman tana gurin mutane, ita tace in rike shi" Mommy ta mika mata hannu "bani shi in gani, watakila diaper za'a chanja masa ko kuma kaya ne suka yi masa yawa" yarinyar ta zo ta mika mata shi ta karbe shi and she laughed and said "wow, ina karbar yaron nan sai naga kamar twins sanda suna babies" ta sake jujjuya shi a hannunta and she looked at me, muna hada ido na sunkuyar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna, ta sake kallon sa ta kalle ni a take na fahimci ta gane shi. Ta juya tana kallon yarinyar tace "dan waye?" kanwar Aunty Hajjo da suke tare tace "au wai kema baki san ta haihu ba? Dan Hajjo ne fa. Matar nan babu wanda ta gayawa tana da ciki kawai sai kiran mu tayi tace ta haihu. Kin san in aka girman nan in Allah ya kawo rabo sai kiga ana jin kunyar fada ana gain kamar abin kunya ne" Mommy ta mika wa matar shi tace "haka ne. Allah ya raya shi", Matar tace ameen sannan ta tashi ta jefa shi sama ta chafe shi, naji kamar zuciyata zata fado kasa, shi kuma ya takarkare ya chanyara kuka, sai kuma ta rungume shi a kirjinta tana dariya sai tace "yaron nan ajebo ne, bai san cika masaki ba. Bara inje in yi masa wanka in goya shi, bacci yake j" tana tafiya Mommy ta juyo tana cigaba da kallona, fuskarta na nuna alamun bacin rai. Sai kuma ta mike tayi hanyar waje tana cewa da sauran mutanen gurin "na tafi. Allah ya bamu alkhairi, idan Hajjo ta shigo kuce mata na tafi" na mike nima da sauri na dauki jakata da waya ta nabi bayanta. A hanyar fita muka hadu da Aunty Hajjo tana shigowa cikin gidan, ta yiwa Mommy magana amma Mommy ko kallon ta bata yi ba, muka kalli juna ni da ita and she understood what happened sai ta bi mu a baya "Sa'adatu naga sako na gode Allah ya bar zumunci, Allah kuma ya huta gajiya, sai munyi waya insha Allah" stil bata ce mata komai ba ta shiga mota, na russuna nace "Aunty mun tafi Allah ya sanya alkhairi" sannan nima na zagaya drivers seat na zauna na tayar da motar muka fita fully knowing that mai raba Mommy da ni ranar sai Allah. Amma sai naji tayi shiru bata ce komai ba. Fuskarta cike da bacin rai. Sai naji babu dadi, na saba da in nayi mata laifi zata yi ta min fada ne ba wai tayi fushi da ni ba. Har muka je gida bata ce min komai ba, nayi packing sannan na juyo ina kallonta nace "Mommy am sorry" ta juyo tana kallona tace "no, don't be. Ba laifinki bane ba ai. Laifi na ne" sannan ta bude motar ta fita. I thought about following her inside in sake bata hakuri but sai na chanja shawara na juya mota na fita, dan bana cikin mood din bata hakuri ina tsoron kar in sake kwafsawa again. Washegari ta koma Kano gurin Daddy, A haka ranaku suka cigaba da wucewa, satittuka suka shude, har aka yi six weeks da bikin mu da Mukhtar amma ya ki bani damar aiwatar da plan B dina a kansa. And for my plan B ina bukatar getting close to him. Akwai ranar da nayi niyyar zuwa dakinsa ma cikin dare in ritsa shi yana bacci amma sai na tarar ashe kofar dakin ma rufe ta yake yi. Wato bashi da niyyar taking any chance with me. Ya kan shigo gurina kusan kullum da assuba, ko da safe idan bai fita da assuba ba, amma a bakin kofar dakina yake tsayawa "good morning sweetheart. Hope babu abinda yake damun ki. Aiki ya matsa min a office ki dan kara yi min hakuri, soon everything will be over kinji? I will soon plan us a vacation" Ko da wasa baya shigo wa cikin dakin, and da ga na taso zuwa gurinsa zai juya ya fita. He never let me gets two meters close to him. Abinda na fahimta bayan rashin gaskiyar sa shine muguwar sha'awa na damunsa, and he chose to avoid me akan yay letting his guard down. I knew he was trying to get rid of the scar and duk ranar da ya samu yayi hakan he will come for me. Wannan kuma shine abinda yake keeping me up wide awake at night. A cikin six weeks din abubuwa da yawa sun faru. Har lokacin Mommy fushi take yi da ni, dan in ba ni na kira ta a waya ba ta daina kira na. Daddy kuma ya matsa min lallai in koma bakin aikina, na fahimci he was worried about me and the way da yake jin sound of my voice a cikin waya yana ganin in na koma aikin it will keep my spirit up, gani yake kamar zaman bana yin komai ne ya jawo nake cikin damuwa. Na ce masa ya dan kara hakuri kadan na kusa komawa, but he didn't believe me sai gashi ya turo uncle Ahmad har gida wai yazo yayi min magana in cigaba da abubuwan da na fara a office. Na gaya masa shima soon zan dawo, akwai abinda nake jira ne. Sai da ya tashi tafiya sannan yace "Safiyya wannan gidan naku yayi muku kadan. Ya kamata ku samu babba ku siya ku koma tunda in kika koma bakin aikin ki ai mutane zasu ke zuwa gurinki, manyan mutane, this house shouldn't be presented as yours" nayi mamakin maganar sa amma sai nace masa "okay babu komai. Za'a sayi wani insha Allah" ya yi murmushi '"a fara duba muku?" Na girgiza kaina "later.…. In lokacin siyan yayi i will talk to you". And then one fateful day, ina zaune akan sallaya ta da daddare na gama shafa"I da wutiri ina adduoina naji shigowar motar Mukhtar, ban wani mai da hankali akan hakan ba dan nasan ba lallai ne ma ya shigo ta nan falon ba, amma ga mamaki na kawai sai ji nayi an bude kofar dakin da nake ciki, na dan tsorata kadan dan ban saka ran shigowar sa ba, nayi sauri na shafa adduar na juyo na ganshi a tsaye a bakin kofa, ya rungume hannayensa a kirjinsa with that smile that I now so much understand a fuskarsa. Naji kirjina ya buga da karfi, tsoro ya kamani but I tried as much as I can to keep my face neutral, nace "you scared me, me kake yi anan kuma yau?" ya gyara tsayuwarsa "hello sweetheart, sorry na baki tsoro, laifi ne dan miji ya shigo dakin matar sa da dare?" na fara dauke kayan sallata nace "au dama ni matar ka ce, ai ni har na manta ma. Thank you for reminding me" yayi dariya tare da karaso wa cikin dakin "kiyi hakuri, I know I haven't been a good husband, but believe me things are going to change a gidan nan from today" na jawo drawer, pretending kamar sallaya nake sakawa a ciki, na dauko abinda zan dauka a ciki na boye a cikin hijab dina na juyo tare da bata rai nace "ka riga kayi wasa da damarka ai Mukhtar, I gave you a golden opportunity ka debi kasa ka watsa min a fuska, yanzu mun riga mun wuce wannan stage din" na fada meaning every word of what I said. Ya fara tahowa zuwa inda nake "na san nayi ba dai dai ba, and believe me it hurt me more than it did you, why do you think na daina zama a gida? It was because I couldn't get that site out of my head, it drove me crazy, it is still driving me crazy. Bana son in hurting dinki, especially after what you went through shi yasa na baki chance dan ki warke sosai. But get ready" ya fada smirking "because I am ready". Na yi getting ready din kuwa exactly like he said, but not in the way he meant, and I watched him come closer har yazo gabana ya tsaya idonsa yana bin jikina da kallo duk kuwa da cewa still akwai hijab a jikin nawa, ya tsaya so close har ina iya jin saukar numfashinsa a fuskata yace "I have dreamt about this night Safiyya, fiye da adadin da zan iya lissafawa, I have planned for this night Fiyya more times than I can remember, for years na yi dakon soyayyar ki a raina mai tarin yawan da ban san adadin ta ba. And tonight, finally, burina zai cika, I am finally going to make you mine, tawa ni kadai, har abada". Na mayar masa da murmushinsa, sannan nace "I also have been planning for this night Mukhtar, amma not for years but for weeks" And then just as I said that, allurar da nake rike da ita a cikin hijab dina ta huda hijab din nawa, ta huda kayansa, ta huda tsokar cinyarsa sannan na juye masa abinda yake cikin syringe din a jikin sa. It happened in seconds, and it was done before he realize what was happening. The next second na matsa da sauri away from him nayi hanyar bakin kofa na tsaya ina kallonsa, ready to run dan jininsa yafi karfin allurar, Ya juyo yana kallona hannunsa rike da cinyarsa, fuskarsa cike da mamaki " Safiyya!" ya ambata idanunsa suna juyewa, "What have you done?" yayi taku biyu zuwa inda nake yana miko hannunsa gare ni, sannan yayi taku daya baya, na dawo cikin dakin na karasa gaban shi na tsaya daf dashi sannan nace "| am giving you the taste of your own medicine" sai kuma na saka hannayena biyu da karfi na tura shi ya fada kan gadon da baya, and he lost consciousness a lokacin. My thought was drugging Mukhtar will be the hardest part of plan B, amma sai bayan da na same shi unconscious akan gado na sannan na fahimci it was the easiest. My plan was to use my handcuffs in daure hannayensa a both sides of the bed and then strip him naked in duba abinda nake nema. Zan daure hannayensa ne saboda ban san karfin jinin sa ba ina tsoron kar ya tashi kafin in gama abinda nake yi. Amma sai lokacin na fahimci cewa karfi na bai fi cikin cokali ba, ba karamar wahala na sha ba kafin in jashi zuwa position din da zai bani damar dare hannayensa duk biyun. Kuma nayi hakan ne cike da tsoro ina gain zai iya farkawa anytime. Bayan na gama sai da na tabbatar handcuffs din sunyi locking hannayensa completely sannan na zauna na huta na sha ruwa sai na fara next task dina na checking his body for the scar, target dina dama shine bayan sa da cinyoyin sa, sai kuma a lokacin na fahimci cewa ba zan iya cire masa rigar ba saboda yadda hannayen sa suke daure, so I got a razor blade and cut it, na yanke ta daga jikin sa sannan na yanke singlet din ciki, and it took me a whole lot of another energy to roll him to his side dan in samu ganin bayan. 1 already had a mental picture of yadda marks din zasu zama, zasu zama size din tsinin fork guda hudu a jere, distance din tsakanin su kuma zai zama even. I checked, bayan fitilar dakin da kuma bedside lamp da na kunna har sai da na kara da fitilar waya ta but banga komai makaman in hakan ba. Wannan ya saka na koma next gurin da nake suspecting, cinyoyin sa, na zare wandon jikinsa na barshi da gajeren, I wasn't looking forward to cire masa gajeren wando for my own mental health, but at the end I had to cut them too, na yanka sides dinsu but leaving the rim and the middle covered dan bana san ganin abinda zai kara min trauma akan wacce nake facing already. Amma babu marks babu alamun su. And then just as I was about to give up I saw something, a scar, a can saman cinyarsa ta hagu kusa da hip bone dinsa, amma kuma wannan sabon tabo ne and it looks nothing like tabon fork. It looks like an yanke a gurin deep yanka wanda har sai da aka yi dinki a gurin. Na sake haska fitila ta sosai sai naga tsahon yankan dai dai fadin yatsun fork ne. It looked new, bana jin zaiyi wata biyu. A lokacin ne na tuna cewa da hannun dama na ji masa ciwon, meaning tabon should be a bangaren hagun sa. Sai na fahimci abinda ya faru, na ja da baya na zauna akan side drawer ina kallon sa cikin bacin rai. Tabbas shine. And that tabon stitches da na gani shine dai dai gurin da ya kamata ace naga tabon fork, but bayan na kwafsa ranar da aka kawo ni na nuna masa alamar cewa ina zarginsa, he got rid of the original scar by creating another one a dai dai inda waccan take. He cut himself. He cut himself deeply and took himself to hospital yayi musu wata karyar suka yi masa dinki a gurin. Wannan ya sa ya ja baya da ni, giving himself time to heal, giving the new scar time to form and cover the old one. And that got me furious, really furious that karfin addu'a he kawai ya rike ni ya hanani hallaka Mukhtar a cikin daren nan. Plan B ya kare. My plan B was to get Mukhtar close and drug him ya zama unconscious, in daure shi yadda ba zai farka yayi harming dina ba, and check for the scar. In na gani kuma in hada kaya na inyi gidan mu and then sue him for rape. Sai dai wannan discovery din ya tabbatar min da cewa to get justice from him dole sai na shiga plan C and I wasn't looking forward to it, duk wannan wahalar da nasha da risking rayuwata was to avoid the plan C. Bana son in shigar da Junior cikin maganar, idan da zan samu yadda nake so, bana son ko sau daya Mukhtar ya dora idonsa akan sa. But now he must come in to get justice for the two of us. Har lokacin Mukhtar bai tashi ba, ya kamata ace hankali na ya tashi amma bai tashi ba, sanda ina neman drug din I asked for mai matsakaicin karfi with low risk dan bana son jininsa a hannuna duk kuwa da cewa chances are higher na cewa jinin sa zai fi karfin maganin but it now seems like jinin na sa bashi da karfi. While waiting sai na dauko red permanent marker din da na ke ajiye da ita a cikin jaka ta na koma kan gadon nayi masa rubutu manya akan goshinsa "RAPIST" sannan na sauko. Na dauko karamar akwati ta da hada duk abubuwan da na san ina bukata, dama kayan sawa kusan duk wadanda suke dakina a Abuja ban dauko ko set daya ba suna can, akwatinan lefe na kuwa har yanzu ko buda su banyi ba. Na ajiye akwatin a gefe na jawo kujera na zauna na saka Mukhtar a gaba ina jiran ya tashi. Sai da sanyin asuba ya fara kadawa sannan ya fara motsi, I saw him trying to open his eyes, sai da kyar ya samu ya bude su sannan ya sauke su a kaina. I smiled and said "hello husband" nan da nan naga toro ya cika fuskarsa, da sauri ya kalli hip dinsa na hagu gurin da scar din yake and then tried to get up. Sai lokacin ya lura da cewa a daure yake "safffiyya" ya fada muryarsa cike da tsoro, "what have you done? Me kika yi min?" Na gyara zama na nace "well, first I drugged you like you did me. But unlike you, I didn't rape you, couldn't even bring myself to look at it. But I saw it, I saw what I was looking for" ya sake kallon gurin sannan ya kalle ni "what? What are you talking about? Wacce maganar kike yi haka? Are you crazy? Get me out of this things?" Ya fada yana jan handcuffs din but he was still very weak bashi da karfi sam. Na mike tsaye na taka gadon da kafa daya looking down at him nace "stop trying, ba zaka fita daga cikin handcuffs din nan ba sai na gama da kai, and am not yet done with you. I don't need a confession out of you saboda already na riga na tabbatar kai ne. You may have temper with the evidence but believe me you are going down one way or another. I promised you dama didn't I? I promised I will take your life just like you took mine. And that's exactly what I am going to do". Ya girgiza kansa pretending to not understand maganganu na "me kike magana akai ne Safiyya? Are you saying ni kike zargi for that? How can you even think that?" Na koma inda na ke zaune na sake zama nace "ba zargin ka nake ba Mukhtar, na tabbatar kaine, kaima kuma kasan na san kaine, that was why you try to get rid of the scar by cutting yourself. So kake in cigaba da zama da kai a matsayin mijina even after knowing what you did to me, So kake in rasa hujjar da zan raba aure na da kai in kuma rasa evidence din da zany convicting dinka in the court of law. But I am already two steps ahead of you Mukhtar" na fada sannan na sake mikewa na dauko handbag dina yayin da shi kuma ya kama rantse rantse "wallahi Safiyya ba ni bane ba. How can you even think nine? I can never hurt you ke ma kin sani because I love you. I love you more than anything Safiyya please ki yarda da ni. Wallahi...... And his words stopped in his throat sanda ya ga abinda na fito da shi daga jaka ta. A brand new scissors. Na bare shi daga cikin ledar sa sannan na saka hannu na nayi testing kaifin sa, na juya ina kallon sa and I have never seen anyone looking as scared as he did, idonsa kamar zasu fado kasa. He tried to get up amma jikin sa was still weak, he tried to get his hands out of the cuff amma shima ya kasa, "Safiyya? Are you crazy? What are you doing? Ki dawo cikin hankalin ki Safiyya. Don't do something stupid out of anger" ya fada yana kokarin juya wa, trying as much as he possibly can to hide the thing in between his legs, Na dawo inda yake na dora kafata daya akan gadon still hannuna rike da almakashin, "why are you afraid? Tsoron me kake ji? The pain? Har yanzu ina tuno da pain din da naji, har yanzu in na rufe ido na ina jin pain din har cikin kwakwalwa ta" '"don't do this Safiyya" ya sake fada frantically trying to free himself, ha cigaba da cewa "relax, I am doing you and the world a favor, in na cire kaga shikenan matan duniya sun huta da hali irin naka, kai ma kuma ka huta da shan wahalar finding your next victims. This is justice for all the girls you have defiled". Cikin tashin hankali Yace "wallahi, I have never touched any girl except you. Only you" na tsaya ina kallon sa "only me? Why me?" Ya fahimci cewa yayi confessing, ya kara rikicewa "I can explain. Please Safiyya ki kunce ni. Ki tsaya muyi magana. Dan Allah Safiyya" a mayar da almakashi na cikin ledar sa nace "i am not going to use this, at least not today and I don't need your explanation. You can explain to Daddy and to the judge" na mayar da almakashin cikin jaka ta, naga yadda hankalin sa ya kwanta, na fahimci sosai yana son toy din nan na sa. Yace "we don't need to do this Safiyya. I have already regretted more than you know, I want to make it up to you, I will make it up to you Safiyya. I will love and take care of you forever. Dan Allah...... You are my wife now Safiyya.... Dan Allah....... Nobody need to know" ban saurare shi ba na cigaba da abin da nake, na gama rufe jakata na rataya na kama handle din ta kayan na rike nace "goodbye Husband" ya cigaba da kokari "get me out of these cuffs mana, don't leave me naked and like these" har na juya zan fita sai kuma na juyo nace "you know what? I have been trying to change from good girl to bad girl, amma har yanzu na kasa, I am good and will always be good. Dan haka zan baka options, ka zabi wanda zan kira maka ya cire ya bude maka cuffs din" na fada ina jefar da keys din a kasa a bakin kofa, na cigaba '"tsakanin Abba, Umma, Yaya, Salim ko Salima, ka zabi daya" ya girgiza kai da sauri "not them... not like this ... Ki dauki waya ta ki kira friend dina Mus'ab. Ko ki bude ni da kanki. Dan Allah Safiyya…... Dan zumuncin da yake tsakanin mu. Don't let them see me like this" na sake dawowa ina kallon sa nace "like what? Naked and in shame? You drugged me, raped me and took me home to my father. Har yau bai sake yarda da ni ba. Har yau bai yarda cewa ba shaye shaye nake yi ba, Har yau bai yarda cewa ba yawon banza nayi na samu ciki ba. And you don't want yours to see you naked?" Ya girgiza kai "Please believe me Safiyya, ban dauka abin zai kai haka ba. Ban san zai gane ba. Ban san zai dauka a buge kike ba. Ban san zaki samu ciki ba. Dan Allah ki yarda, dan Allah ki tsaya muyi magana" ya fada hawaye yana bin gefen fuskar sa. na hadiye dacin da yake makogwaro na nace '"ba ka san zai faru ba, but ya faru, and nothing will change that, nothing will bring me back what you took" na dauko waya ta nace "are you going to choose or should I choose for you? Maybe Umma? I bet she will be very happy that her son is a rapist. You have three seconds.. 1, 2...". Da sauri yace "yaya, call yaya" na mayar da wayar jaka nace "sai nayi bacci na tashi tukunna" sannan na juya na kai bakin kofa ya sake kira na, na tsaya ban juyo ba, yace "think about this one last time, do you really want to do this? It is going to be my words against yours" na juyo da fuskata ina kallon sa nace "'no husband, it is going to be your words against yours" Maman Maama✍🏻[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty One: "Goodbye Husband" Al'ummar jihar Jigawa da kewayenta har ma da jihohin kusa . Haifa foods and pastries ta zo muku da kayan maqulashe kala kala irin su yogo fura wanda babu kamar sa ga dadi ga qoshi ga gardin shi badaganan©️ wani abun saima ka dandana. Ga irin su milk cake (sunan wani abu wai farfesun madara) wanda babu kamar shi ga sauqi ga dadi, cocunut milk wanda har getare babu kamar shi da kuma uwa uba Yogo fruits wanda ze gara muku Ify. Zaku sami kayan HAIFA har kofan gidajenku in kuna so ga komai na HAIFA a farashi mai sauki yake ku garzaya ku dandana kayan dadin Haifa 0812 536 8737 https://www.instagram.com haifa_foods_and_pastries iigsh=NHYyN2k1eTlhenBt&utm_ source=gr *. *. *. *. Ina kallon sanda ya hadiye wani mugun yawu sannan ya fara girgiza kansa, "What are you doing Fiyya. Na gaya miki baki da lafiya. I don't want to hurt you" na fara cat walking zuwa inda yake tsaye "really? Even if that's the case then we will be careful. I know you will not hurt me. I trust you" na tsaya half way from him, studying yadda yake bina da kallon, yadda idanunsa suke juyewa, and I hated myself for doing that. But I have already started dan haka sai na karasa. Na saka hannu na sauke kafadar rigar jikina guda daya, it slid down my arms and exposed more of my skin, he started taking steps toward me and I gave him a look da nake tunanin is seductive and turned around, signalling him with my hand to follow me sannan cikin tafiyar da na tabbatar ba zai iya resisting ba na koma dakin da na fito daga ciki. Ina shiga na kalli gadon da sauri making sure cewa the handcuffs I kept locked at each side of the bed suna nan but completely hidden sai dai in kasan da zaman su, na san cewa wasa nake da wuta kuma probability is very high that wutar zata kona ni but I was ready to get burnt in dai zan samu abinda nake bukata, Sai dai kuma zuciya ta da gangar jiki na cike suke da tsoro, kayan ciki na har karkarwa suke yi. Naji shigowar sa nayi sauri na juya dan bana so in dauke ido na daga gare shi even for a second. Ya tsaya a bakin kofa yana cigaba da kallo na, and akwai wani murmushi da na kasa fahimta a lips din shi. Ya karasa shigowa "you are seducing me" ya fada directly, but daga muryarsa na san I got him right where I wanted him. Nayi kokarin yin magana but abinda kawai yake kwakwalwa ta was that night, the pain, the darkness, the fear, the........ "Are you sure you know what you are getting yourself into?" Ya sake fada, bitting his lips. Nayi taku biyu zuwa gareshi "is it a crime idan mata tayi seducing mijinta? I am not made of stone and I have a husband. Besides, you promised me a show ranar nan, I want to see the complete show". Ya karaso gaba na, looking down at me "you want a show? You really want a show? You will have a show" ya fada muryar sa a cikin kirjin sa sannan ya dora hannayensa akan kafaduna tare da kokarin jawo ni closer to him at the same time trying to kiss me. All | wanted a lokacin was to scream on top of my voice, to scream out all my anger and hatred for him, to stab him in one place or two, amma instead sai na zame daga gare shi na koma kan gado na zauna, close to the spot da na makala one of my handcuffs. Ya juyo yana kallo na, sai kuma ya tafi gurin light switch ya dora hannunsa akai da niyya kashewa. Na mike da sauri, "Please, no, I hate the dark. It scares me" and I meant that har cikin raina. Ya juyo yana kallona and I saw him shakes his head sannan yace "no!" Na kara matsowa "please leave the light on" sai ya matsa daga kusa da ni ya sake cewa "no" na tsaya kawai ina kallon sa, na fahimci guduwa yake shirin sake yi ya juya min baya da sauri trying to stop looking at me "no, you are sick, and we shouldn't do this sai kin warke" yana gama fadar haka yayi hanyar fita da sauri. Na bishi nima da sauri na kama hannun sa da hannu daya sannan na juyo da fuskar sa da daya hannun "i am not sick, come, will show you that I am fine" and then he smiled at me, a smile that confirmed all my suspicious "not tonight, sweetheart" sannan ya juya ya fita. Na koma da baya har sai da kafafuwa na suka ta ba gadon dakin sannan na zauna akan sa. Yanzu shikenan? I have belittled myself for nothing? Amma kuma sai naji wani relief a wani bangaren zuciya ta, I wasn't sure my plan A will work and wannan abinda ya faru ya tabbatar min da cewa plan A is off. Dama na shirya plan A din ne saboda akwai remnants of shakku a zuciya ta na cewa shi ya aikata min wancan laifin. Bana son in dauki alhakin sa idan shi innocent ne and I risked everything to avoid that. Amma yanzu, the way he rejected me bayan na san babu abinda yake so irin to have me, ya tabbatar min da cewa shi din dai shine. Ba fariya ba, yadda Allah ya tsara jikina, dan ma dai har yanzu ban dawo yadda nake ba, ba Mukhtar da ya jima yana lusting for me ba, bana jin akwai namijin da zan bude masa jikina kamar yadda na bude wa Mukhtar yau, sannan mu shiga daki daga ni sai shi, sannan ga igiyar aure uku a tsakanin mu, kuma ace yayi rejecting dina yayi tafiyarsa. Wannan ya kara tabbatar min da abu uku, na farko Mukhtar ne yayi raping dina, na biyu kuma ya san ina zargin shi, na uku and the most important thing shine the scar is there, A yadda na bashi labarin daren da akayi raping dina in details ya tabbatar masa da cewa ina cikin hayyacina sanda na ji masa ciwo, and the way that I tried seducing him tonight bayan halin ko in kula da nake nuna masa kafin in tare ya tabbatar masa da cewa shaida nake nema a kansa, kuma wannan scar din ita ce shaida. Wannan realization din kuma sai yay unblocking another fear in me, he will now try to get rid of the scar ta kowanne hali. Tunda a ganin sa ita kadai ce shaidar da zata tabbatar min da kuma duniya cewa shine. Musamman tunda yana tunanin Junior ya mutu. And that was where I had upper hands in the matter, na kuma gode Allah da yasa nayi wancan tunanin dan in da yasan Junior yana raye kuma ya san ina zargin sa zai iya kokarin ma kawar da ni daga duniya to cover his crime. Wannan daren shine ya kawo karshen plan A dina. My plan A was to seduce him to my bed, handcuff both his hands idan na dauke masa hankali da jikina, and then check his body for the scars. It was risky but worth a trial considering bani da tabbas din shine dan haka bana son cutar da shi. Yanzu kuma it is going to be an eye for an eye. Dan yanzu zamu shiga plan B. Sai dai kuma daga alama shima Mukhtar ya chanja takunsa gabaki daya. Dan ganin shi ma daga ranar gagara ta yayi. Da asuba yake fita, sai cikin dare kuma yake dawowa, wani lokacin ma in ya tashi dawowa ta can daya kofar falonsa yake shiga zuwa dakinsa sannan in zai fita ma ya fita ta can. Mun koma kamar mage da bera a cikin gidan auren mu. And that frustrate me more than anything. Kamar yadda nayi alkawari ba zan yi girki a gidan Mukhtar ba, ban taba dafa ko da noddles ba, order abinci nake yi kuma a kawo min har gida. Shima kuma bai taba tambaya ta abinci ba, ban san kuma inda yake zuwa ya ci ba. And I didn't care. Bai taba kawo abokansa gidan ba, nima kuma ban gayyaci kawayena ba duk kuwa da korafin da suka ringa yi min a waya cewa anyi bikina amma ban gayyace su ba kuma gidan nawa ma ban gayyace su ba, I told them suyi hakuri abin ne yazo min lokaci daya amma na yi musu alkawarin shirya musu walima wata rana. Amma na fada musu hakan ne dan su rabu da ni inyi concentrating akan abinda yake gaba na. Sati biyu da biki na aka yi na Abdul. Tun kafin bikin na kira shi a waya nayi masa murna tare da lallaba shi da kyar ya turo min account details dinsa and I sent him heavy da sai da uncle Sufyan da kansa ya kira Daddy and Daddy said babu ruwansa ni nayi niyya kuma tsakanin mu da Abdul ne. Lokacin bikin Abdul Mommy tazo gari, dama munyi waya da ita tace min in shirya zata zo muje gidan bikin tare ni da ita da Safina, and I wasn't looking forward to that. Nayi ta neman hanyar da zan zame in fasa zuwa na rasa kuma gashi ina son zuwa din ko dan Aunty Hajjo, na san zata ji dadi sosai idan naje. But I was in no mood to neither meet nor talk to Safina. Sai dai cikin ikon Allah ranar da Mommy ta zo gari take gaya min Safina ba zata samu damar zuwa ba, bata da lafiya, "gashi shi kuma mijin nata har yanzu bai dawo ba, ina tunanin da ita zan koma Kano gaskiya, gwara in san a gabana take, ko kuma in je gidan iyayen nasa inji me zasu ce, amma wannan ai ba aure ba ne ba" ban ce komai ba kuma banyi niyyar cewa komai ba, sai kuma tace "ya kamata dai kije ki duba ta" nace "insha Allah". Amma sai naji dadin cewa ba zan hadu da Safina ba, Ranar yini Mommy tazo ta dauke ni muka je tare. I kept thinking ko zamu ga Junior? Ko zata gane shi? Amma da yake a event center akayi bikin I guess Aunty Hajjo bata tafi da shi ba dan duk baza ido na ban ganshi ba. Washegari da dare muka sake zuwa dinner. Aunty Hajjo taji dadin ganin mu sosai kuma ta karrama mu sosai, naje har gurin ango da amarya na taya su murna and they looked so happy and so in love with each other. Abdul yayi introducing dina a grin amaryarsa muka gaisa sosai, yana tsokana ta wai ina ango na. Sai ganin su naji ya fama min wani ciwo a zuciya ta da nake ta ajjiye da shi, and as I sat down looking at them I thought about him, ko ina yake? Ko me yake ciki? And I so much wanted to unblock his phone number and call him, maybe inyi pretending kamar babu abinda ya faru and say '"tsokanar ka fa nake yi Yaya Muhammad. It was all a prank. I miss you so much", I remembered the sound of his voice over the phone, the deepness of it and how it has always reach deep into my heart "hey Piya, you have no idea how much I miss you" na sunkuyar da ido na kasa ina jin hawaye yana taruwa a idona, a hankali nace "I miss you too Yaya Muhammad". A lokacin ne naji Mommy tana taba ni "Kinga mother in law din Safina, Ashe ta san su Sufyan" nayi sauri na dago kai and I saw her tana tafiya zata zauna. Ban taba ganin ta ba amma na tabbatar ko da kuwa Mommy bata nuna min ita ba zan iya gane ta idan na ganta. Kana ganin ta indai kasan Muhammad to zaka san cewa ita ta haife shi. Mommy ta ja hannuna "zo muje ku gaisa da ita" na zame hannu na tare da langwabe kai "Mommy please" tace "ke fa matsalar ki kenan ba kya son mutane, ai sai kiyi ta zama" ta tafi ta barni. Nayi ajiyar zuciya na cigaba da kallon Mama da ga nesa, naki zuwa ne saboda ina jin toro, ban sani ba ko ta taba ganin hotona a wayar Muhammad ko something like that, ina tsoron kar ta gane ni, duk da dai na san karin maganar hausawa da suke cewa idan kere na yawo zabo na yawo watarana dole za'a hadu. Wasa wasa dai sai naga Mommy ta samu kujera a can ta zauna sun cigaba da hira. Ni dai ina zaune a guri daya har aka gama sannan Mommy ta zo muka tafi. Tun kafin mu fita na san cewa I was in for hirar Safina da mijinta har muje gida, ai kuwa dai muna shiga mota ta fara "mutanen nan suna da son kansu wallahi, kinji wai basu san Safina babu lafiya ba, wai bata gaya musu ba shima bai gaya musu ba, Amma dai munyi magana tace zata je gidan ta dauke ta ta mayar da ita can gabanta su zauna tare kafin mijin ya dawo. Ai ce mata kawai nayi tafiya zanyi da Safina Kano inyi jinyar ta a can" naji kamar in toshe kunnena irin yadda nake mata in bana son jin maganar da take yi sai kuma na fasa, tunda na mayar da zargina kan Mukhtar a fara sassautowa akan Mommy. Sai kuma tayi ajjiyar zuciya tace "ni tausayi take bani yarinyar nan, Allah ya sassauta mata wanna lamarin. Ko babu komai iyayensa masu kirki ne". Ranar daurin aure ma muka sake komawa gidan Aunty Hajjo, ranar ni na fara fita a motata naje na dauki Mommy sannan muka wuce, muna yin packing na dauko envelope din dana taho da ita da kudi masu kauri a ciki na mika wa mommy nace "gashi Mommy ko zaki bawa Aunty gudummawa" ai kam taji dadin haka sosai "kai amma kin kyauta Safiyya, dama ina ta tunanin abinda zan bata na rasa" nayi murmushi kawai na fita. Ranar babu mutane sosai tunda daurin aure ne, sai yan uwansu na jiki sai kuma few close friends kamar mu. Muka zauna a falo Mommy ta samu wata yar uwar Aunty Hajjo itama mai surutu suna ta zance ni kuma na koma gefe ina ta rubuta wani sabon plan da nake shiryawa akan maganar reopening Oasis da nake son yi as soon as I get rid of Mukhtar. Muna nan sai ga wata yarinya ta shigo falon da Junior a hannunta, tazo ta zauna opposite din su mommy ta na bashi madara shi kuma yana ta rigima yaki sha sai dawo da ita yake yi. Na ajiye waya ta akan cinyata ina kallon su. Kanwar Aunty Hajjo ta juya gurin su itama tace "ke Husna yaron nan fa ya koshi, daga alama bacci yake ji ki goya shi mana" wadda aka kira da Husna ta kwabe fuska kamar zata yi kuka tace "na goya shin fa yaki yin baccin wallahi. Wannan yaron rigimamme ne" Mommy ta juya tana kallon su ita ma sai tace "ki kaiwa maman sa shi mana to, maybe goyon ne baki iya ba" yarinyar tace "to ai maman tana gurin mutane, ita tace in rike shi" Mommy ta mika mata hannu "bani shi in gani, watakila diaper za'a chanja masa ko kuma kaya ne suka yi masa yawa" yarinyar ta zo ta mika mata shi ta karbe shi and she laughed and said "wow, ina karbar yaron nan sai naga kamar twins sanda suna babies" ta sake jujjuya shi a hannunta and she looked at me, muna hada ido na sunkuyar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna, ta sake kallon sa ta kalle ni a take na fahimci ta gane shi. Ta juya tana kallon yarinyar tace "dan waye?" kanwar Aunty Hajjo da suke tare tace "au wai kema baki san ta haihu ba? Dan Hajjo ne fa. Matar nan babu wanda ta gayawa tana da ciki kawai sai kiran mu tayi tace ta haihu. Kin san in aka girman nan in Allah ya kawo rabo sai kiga ana jin kunyar fada ana gain kamar abin kunya ne" Mommy ta mika wa matar shi tace "haka ne. Allah ya raya shi", Matar tace ameen sannan ta tashi ta jefa shi sama ta chafe shi, naji kamar zuciyata zata fado kasa, shi kuma ya takarkare ya chanyara kuka, sai kuma ta rungume shi a kirjinta tana dariya sai tace "yaron nan ajebo ne, bai san cika masaki ba. Bara inje in yi masa wanka in goya shi, bacci yake j" tana tafiya Mommy ta juyo tana cigaba da kallona, fuskarta na nuna alamun bacin rai. Sai kuma ta mike tayi hanyar waje tana cewa da sauran mutanen gurin "na tafi. Allah ya bamu alkhairi, idan Hajjo ta shigo kuce mata na tafi" na mike nima da sauri na dauki jakata da waya ta nabi bayanta. A hanyar fita muka hadu da Aunty Hajjo tana shigowa cikin gidan, ta yiwa Mommy magana amma Mommy ko kallon ta bata yi ba, muka kalli juna ni da ita and she understood what happened sai ta bi mu a baya "Sa'adatu naga sako na gode Allah ya bar zumunci, Allah kuma ya huta gajiya, sai munyi waya insha Allah" stil bata ce mata komai ba ta shiga mota, na russuna nace "Aunty mun tafi Allah ya sanya alkhairi" sannan nima na zagaya drivers seat na zauna na tayar da motar muka fita fully knowing that mai raba Mommy da ni ranar sai Allah. Amma sai naji tayi shiru bata ce komai ba. Fuskarta cike da bacin rai. Sai naji babu dadi, na saba da in nayi mata laifi zata yi ta min fada ne ba wai tayi fushi da ni ba. Har muka je gida bata ce min komai ba, nayi packing sannan na juyo ina kallonta nace "Mommy am sorry" ta juyo tana kallona tace "no, don't be. Ba laifinki bane ba ai. Laifi na ne" sannan ta bude motar ta fita. I thought about following her inside in sake bata hakuri but sai na chanja shawara na juya mota na fita, dan bana cikin mood din bata hakuri ina tsoron kar in sake kwafsawa again. Washegari ta koma Kano gurin Daddy, A haka ranaku suka cigaba da wucewa, satittuka suka shude, har aka yi six weeks da bikin mu da Mukhtar amma ya ki bani damar aiwatar da plan B dina a kansa. And for my plan B ina bukatar getting close to him. Akwai ranar da nayi niyyar zuwa dakinsa ma cikin dare in ritsa shi yana bacci amma sai na tarar ashe kofar dakin ma rufe ta yake yi. Wato bashi da niyyar taking any chance with me. Ya kan shigo gurina kusan kullum da assuba, ko da safe idan bai fita da assuba ba, amma a bakin kofar dakina yake tsayawa "good morning sweetheart. Hope babu abinda yake damun ki. Aiki ya matsa min a office ki dan kara yi min hakuri, soon everything will be over kinji? I will soon plan us a vacation" Ko da wasa baya shigo wa cikin dakin, and da ga na taso zuwa gurinsa zai juya ya fita. He never let me gets two meters close to him. Abinda na fahimta bayan rashin gaskiyar sa shine muguwar sha'awa na damunsa, and he chose to avoid me akan yay letting his guard down. I knew he was trying to get rid of the scar and duk ranar da ya samu yayi hakan he will come for me. Wannan kuma shine abinda yake keeping me up wide awake at night. A cikin six weeks din abubuwa da yawa sun faru. Har lokacin Mommy fushi take yi da ni, dan in ba ni na kira ta a waya ba ta daina kira na. Daddy kuma ya matsa min lallai in koma bakin aikina, na fahimci he was worried about me and the way da yake jin sound of my voice a cikin waya yana ganin in na koma aikin it will keep my spirit up, gani yake kamar zaman bana yin komai ne ya jawo nake cikin damuwa. Na ce masa ya dan kara hakuri kadan na kusa komawa, but he didn't believe me sai gashi ya turo uncle Ahmad har gida wai yazo yayi min magana in cigaba da abubuwan da na fara a office. Na gaya masa shima soon zan dawo, akwai abinda nake jira ne. Sai da ya tashi tafiya sannan yace "Safiyya wannan gidan naku yayi muku kadan. Ya kamata ku samu babba ku siya ku koma tunda in kika koma bakin aikin ki ai mutane zasu ke zuwa gurinki, manyan mutane, this house shouldn't be presented as yours" nayi mamakin maganar sa amma sai nace masa "okay babu komai. Za'a sayi wani insha Allah" ya yi murmushi '"a fara duba muku?" Na girgiza kaina "later.…. In lokacin siyan yayi i will talk to you". And then one fateful day, ina zaune akan sallaya ta da daddare na gama shafa"I da wutiri ina adduoina naji shigowar motar Mukhtar, ban wani mai da hankali akan hakan ba dan nasan ba lallai ne ma ya shigo ta nan falon ba, amma ga mamaki na kawai sai ji nayi an bude kofar dakin da nake ciki, na dan tsorata kadan dan ban saka ran shigowar sa ba, nayi sauri na shafa adduar na juyo na ganshi a tsaye a bakin kofa, ya rungume hannayensa a kirjinsa with that smile that I now so much understand a fuskarsa. Naji kirjina ya buga da karfi, tsoro ya kamani but I tried as much as I can to keep my face neutral, nace "you scared me, me kake yi anan kuma yau?" ya gyara tsayuwarsa "hello sweetheart, sorry na baki tsoro, laifi ne dan miji ya shigo dakin matar sa da dare?" na fara dauke kayan sallata nace "au dama ni matar ka ce, ai ni har na manta ma. Thank you for reminding me" yayi dariya tare da karaso wa cikin dakin "kiyi hakuri, I know I haven't been a good husband, but believe me things are going to change a gidan nan from today" na jawo drawer, pretending kamar sallaya nake sakawa a ciki, na dauko abinda zan dauka a ciki na boye a cikin hijab dina na juyo tare da bata rai nace "ka riga kayi wasa da damarka ai Mukhtar, I gave you a golden opportunity ka debi kasa ka watsa min a fuska, yanzu mun riga mun wuce wannan stage din" na fada meaning every word of what I said. Ya fara tahowa zuwa inda nake "na san nayi ba dai dai ba, and believe me it hurt me more than it did you, why do you think na daina zama a gida? It was because I couldn't get that site out of my head, it drove me crazy, it is still driving me crazy. Bana son in hurting dinki, especially after what you went through shi yasa na baki chance dan ki warke sosai. But get ready" ya fada smirking "because I am ready". Na yi getting ready din kuwa exactly like he said, but not in the way he meant, and I watched him come closer har yazo gabana ya tsaya idonsa yana bin jikina da kallo duk kuwa da cewa still akwai hijab a jikin nawa, ya tsaya so close har ina iya jin saukar numfashinsa a fuskata yace "I have dreamt about this night Safiyya, fiye da adadin da zan iya lissafawa, I have planned for this night Fiyya more times than I can remember, for years na yi dakon soyayyar ki a raina mai tarin yawan da ban san adadin ta ba. And tonight, finally, burina zai cika, I am finally going to make you mine, tawa ni kadai, har abada". Na mayar masa da murmushinsa, sannan nace "I also have been planning for this night Mukhtar, amma not for years but for weeks" And then just as I said that, allurar da nake rike da ita a cikin hijab dina ta huda hijab din nawa, ta huda kayansa, ta huda tsokar cinyarsa sannan na juye masa abinda yake cikin syringe din a jikin sa. It happened in seconds, and it was done before he realize what was happening. The next second na matsa da sauri away from him nayi hanyar bakin kofa na tsaya ina kallonsa, ready to run dan jininsa yafi karfin allurar, Ya juyo yana kallona hannunsa rike da cinyarsa, fuskarsa cike da mamaki " Safiyya!" ya ambata idanunsa suna juyewa, "What have you done?" yayi taku biyu zuwa inda nake yana miko hannunsa gare ni, sannan yayi taku daya baya, na dawo cikin dakin na karasa gaban shi na tsaya daf dashi sannan nace "| am giving you the taste of your own medicine" sai kuma na saka hannayena biyu da karfi na tura shi ya fada kan gadon da baya, and he lost consciousness a lokacin. My thought was drugging Mukhtar will be the hardest part of plan B, amma sai bayan da na same shi unconscious akan gado na sannan na fahimci it was the easiest. My plan was to use my handcuffs in daure hannayensa a both sides of the bed and then strip him naked in duba abinda nake nema. Zan daure hannayensa ne saboda ban san karfin jinin sa ba ina tsoron kar ya tashi kafin in gama abinda nake yi. Amma sai lokacin na fahimci cewa karfi na bai fi cikin cokali ba, ba karamar wahala na sha ba kafin in jashi zuwa position din da zai bani damar dare hannayensa duk biyun. Kuma nayi hakan ne cike da tsoro ina gain zai iya farkawa anytime. Bayan na gama sai da na tabbatar handcuffs din sunyi locking hannayensa completely sannan na zauna na huta na sha ruwa sai na fara next task dina na checking his body for the scar, target dina dama shine bayan sa da cinyoyin sa, sai kuma a lokacin na fahimci cewa ba zan iya cire masa rigar ba saboda yadda hannayen sa suke daure, so I got a razor blade and cut it, na yanke ta daga jikin sa sannan na yanke singlet din ciki, and it took me a whole lot of another energy to roll him to his side dan in samu ganin bayan. 1 already had a mental picture of yadda marks din zasu zama, zasu zama size din tsinin fork guda hudu a jere, distance din tsakanin su kuma zai zama even. I checked, bayan fitilar dakin da kuma bedside lamp da na kunna har sai da na kara da fitilar waya ta but banga komai makaman in hakan ba. Wannan ya saka na koma next gurin da nake suspecting, cinyoyin sa, na zare wandon jikinsa na barshi da gajeren, I wasn't looking forward to cire masa gajeren wando for my own mental health, but at the end I had to cut them too, na yanka sides dinsu but leaving the rim and the middle covered dan bana san ganin abinda zai kara min trauma akan wacce nake facing already. Amma babu marks babu alamun su. And then just as I was about to give up I saw something, a scar, a can saman cinyarsa ta hagu kusa da hip bone dinsa, amma kuma wannan sabon tabo ne and it looks nothing like tabon fork. It looks like an yanke a gurin deep yanka wanda har sai da aka yi dinki a gurin. Na sake haska fitila ta sosai sai naga tsahon yankan dai dai fadin yatsun fork ne. It looked new, bana jin zaiyi wata biyu. A lokacin ne na tuna cewa da hannun dama na ji masa ciwon, meaning tabon should be a bangaren hagun sa. Sai na fahimci abinda ya faru, na ja da baya na zauna akan side drawer ina kallon sa cikin bacin rai. Tabbas shine. And that tabon stitches da na gani shine dai dai gurin da ya kamata ace naga tabon fork, but bayan na kwafsa ranar da aka kawo ni na nuna masa alamar cewa ina zarginsa, he got rid of the original scar by creating another one a dai dai inda waccan take. He cut himself. He cut himself deeply and took himself to hospital yayi musu wata karyar suka yi masa dinki a gurin. Wannan ya sa ya ja baya da ni, giving himself time to heal, giving the new scar time to form and cover the old one. And that got me furious, really furious that karfin addu'a he kawai ya rike ni ya hanani hallaka Mukhtar a cikin daren nan. Plan B ya kare. My plan B was to get Mukhtar close and drug him ya zama unconscious, in daure shi yadda ba zai farka yayi harming dina ba, and check for the scar. In na gani kuma in hada kaya na inyi gidan mu and then sue him for rape. Sai dai wannan discovery din ya tabbatar min da cewa to get justice from him dole sai na shiga plan C and I wasn't looking forward to it, duk wannan wahalar da nasha da risking rayuwata was to avoid the plan C. Bana son in shigar da Junior cikin maganar, idan da zan samu yadda nake so, bana son ko sau daya Mukhtar ya dora idonsa akan sa. But now he must come in to get justice for the two of us. Har lokacin Mukhtar bai tashi ba, ya kamata ace hankali na ya tashi amma bai tashi ba, sanda ina neman drug din I asked for mai matsakaicin karfi with low risk dan bana son jininsa a hannuna duk kuwa da cewa chances are higher na cewa jinin sa zai fi karfin maganin but it now seems like jinin na sa bashi da karfi. While waiting sai na dauko red permanent marker din da na ke ajiye da ita a cikin jaka ta na koma kan gadon nayi masa rubutu manya akan goshinsa "RAPIST" sannan na sauko. Na dauko karamar akwati ta da hada duk abubuwan da na san ina bukata, dama kayan sawa kusan duk wadanda suke dakina a Abuja ban dauko ko set daya ba suna can, akwatinan lefe na kuwa har yanzu ko buda su banyi ba. Na ajiye akwatin a gefe na jawo kujera na zauna na saka Mukhtar a gaba ina jiran ya tashi. Sai da sanyin asuba ya fara kadawa sannan ya fara motsi, I saw him trying to open his eyes, sai da kyar ya samu ya bude su sannan ya sauke su a kaina. I smiled and said "hello husband" nan da nan naga toro ya cika fuskarsa, da sauri ya kalli hip dinsa na hagu gurin da scar din yake and then tried to get up. Sai lokacin ya lura da cewa a daure yake "safffiyya" ya fada muryarsa cike da tsoro, "what have you done? Me kika yi min?" Na gyara zama na nace "well, first I drugged you like you did me. But unlike you, I didn't rape you, couldn't even bring myself to look at it. But I saw it, I saw what I was looking for" ya sake kallon gurin sannan ya kalle ni "what? What are you talking about? Wacce maganar kike yi haka? Are you crazy? Get me out of this things?" Ya fada yana jan handcuffs din but he was still very weak bashi da karfi sam. Na mike tsaye na taka gadon da kafa daya looking down at him nace "stop trying, ba zaka fita daga cikin handcuffs din nan ba sai na gama da kai, and am not yet done with you. I don't need a confession out of you saboda already na riga na tabbatar kai ne. You may have temper with the evidence but believe me you are going down one way or another. I promised you dama didn't I? I promised I will take your life just like you took mine. And that's exactly what I am going to do". Ya girgiza kansa pretending to not understand maganganu na "me kike magana akai ne Safiyya? Are you saying ni kike zargi for that? How can you even think that?" Na koma inda na ke zaune na sake zama nace "ba zargin ka nake ba Mukhtar, na tabbatar kaine, kaima kuma kasan na san kaine, that was why you try to get rid of the scar by cutting yourself. So kake in cigaba da zama da kai a matsayin mijina even after knowing what you did to me, So kake in rasa hujjar da zan raba aure na da kai in kuma rasa evidence din da zany convicting dinka in the court of law. But I am already two steps ahead of you Mukhtar" na fada sannan na sake mikewa na dauko handbag dina yayin da shi kuma ya kama rantse rantse "wallahi Safiyya ba ni bane ba. How can you even think nine? I can never hurt you ke ma kin sani because I love you. I love you more than anything Safiyya please ki yarda da ni. Wallahi...... And his words stopped in his throat sanda ya ga abinda na fito da shi daga jaka ta. A brand new scissors. Na bare shi daga cikin ledar sa sannan na saka hannu na nayi testing kaifin sa, na juya ina kallon sa and I have never seen anyone looking as scared as he did, idonsa kamar zasu fado kasa. He tried to get up amma jikin sa was still weak, he tried to get his hands out of the cuff amma shima ya kasa, "Safiyya? Are you crazy? What are you doing? Ki dawo cikin hankalin ki Safiyya. Don't do something stupid out of anger" ya fada yana kokarin juya wa, trying as much as he possibly can to hide the thing in between his legs, Na dawo inda yake na dora kafata daya akan gadon still hannuna rike da almakashin, "why are you afraid? Tsoron me kake ji? The pain? Har yanzu ina tuno da pain din da naji, har yanzu in na rufe ido na ina jin pain din har cikin kwakwalwa ta" '"don't do this Safiyya" ya sake fada frantically trying to free himself, ha cigaba da cewa "relax, I am doing you and the world a favor, in na cire kaga shikenan matan duniya sun huta da hali irin naka, kai ma kuma ka huta da shan wahalar finding your next victims. This is justice for all the girls you have defiled". Cikin tashin hankali Yace "wallahi, I have never touched any girl except you. Only you" na tsaya ina kallon sa "only me? Why me?" Ya fahimci cewa yayi confessing, ya kara rikicewa "I can explain. Please Safiyya ki kunce ni. Ki tsaya muyi magana. Dan Allah Safiyya" a mayar da almakashi na cikin ledar sa nace "i am not going to use this, at least not today and I don't need your explanation. You can explain to Daddy and to the judge" na mayar da almakashin cikin jaka ta, naga yadda hankalin sa ya kwanta, na fahimci sosai yana son toy din nan na sa. Yace "we don't need to do this Safiyya. I have already regretted more than you know, I want to make it up to you, I will make it up to you Safiyya. I will love and take care of you forever. Dan Allah...... You are my wife now Safiyya.... Dan Allah....... Nobody need to know" ban saurare shi ba na cigaba da abin da nake, na gama rufe jakata na rataya na kama handle din ta kayan na rike nace "goodbye Husband" ya cigaba da kokari "get me out of these cuffs mana, don't leave me naked and like these" har na juya zan fita sai kuma na juyo nace "you know what? I have been trying to change from good girl to bad girl, amma har yanzu na kasa, I am good and will always be good. Dan haka zan baka options, ka zabi wanda zan kira maka ya cire ya bude maka cuffs din" na fada ina jefar da keys din a kasa a bakin kofa, na cigaba '"tsakanin Abba, Umma, Yaya, Salim ko Salima, ka zabi daya" ya girgiza kai da sauri "not them... not like this ... Ki dauki waya ta ki kira friend dina Mus'ab. Ko ki bude ni da kanki. Dan Allah Safiyya…... Dan zumuncin da yake tsakanin mu. Don't let them see me like this" na sake dawowa ina kallon sa nace "like what? Naked and in shame? You drugged me, raped me and took me home to my father. Har yau bai sake yarda da ni ba. Har yau bai yarda cewa ba shaye shaye nake yi ba, Har yau bai yarda cewa ba yawon banza nayi na samu ciki ba. And you don't want yours to see you naked?" Ya girgiza kai "Please believe me Safiyya, ban dauka abin zai kai haka ba. Ban san zai gane ba. Ban san zai dauka a buge kike ba. Ban san zaki samu ciki ba. Dan Allah ki yarda, dan Allah ki tsaya muyi magana" ya fada hawaye yana bin gefen fuskar sa. na hadiye dacin da yake makogwaro na nace '"ba ka san zai faru ba, but ya faru, and nothing will change that, nothing will bring me back what you took" na dauko waya ta nace "are you going to choose or should I choose for you? Maybe Umma? I bet she will be very happy that her son is a rapist. You have three seconds.. 1, 2...". Da sauri yace "yaya, call yaya" na mayar da wayar jaka nace "sai nayi bacci na tashi tukunna" sannan na juya na kai bakin kofa ya sake kira na, na tsaya ban juyo ba, yace "think about this one last time, do you really want to do this? It is going to be my words against yours" na juyo da fuskata ina kallon sa nace "'no husband, it is going to be your words against yours" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Two: Shattered Desires Not Edited. Ina fita na shiga mota ta na tayar a dai dai lokacin da mai gadin gidan yake kokarin yin alwala, ya ajiye butar hannunsa da sauri ya taho inda nake "Hajiya..... Allah dai ya sa lafiya" nace "lafiya lau, zan yi tafiya ne kuma jirgin mu in an jina kadan zai tashi" ya gyada kai cikin fahimta amma kuma sai yace "ai da mai gidan ya raka ki Hajiya, garin ne kin san yanzu sai a hankali. Ina ji miki tsoron fita ke kadai" na kirkiri murmushi nace "nayi addu'a. Now, bude min gate" na karasa maganar da authority a voice dina, ya juya da sauri yaje ya bude gate din na ja mota ta na fita. Gidan mu na zarce direct, na tarar mai Eta gadin mu ya davo daga masallaci kenan yana shirin bude gate sai ya ga mota ta, ya gane motar amma sai ya fasa bude kofar ya dawo da baya yana kara kokarin ganin wanda ya ke cikin motar, na sauke tinted glass din windon motar dan saukaka masa gani na. Yayi sauri ya sussuna "sannu da zuwa ranki ya dade" ban ce komai ba sai na mayar da window na rufe, ya ruga da sauri ya bude gate din ni kuma na shiga da motar ciki nayi packing dinta a gurin da dama nan ne inda nake ajjiye ta. Na sauke ajjiyar zuciya sannan na bude kofa na fito, mai gadin ya karaso inda nake yana kallo na da hasken alfijir da ya fara haska gari, "sannu da zuwa, da assuba haka? Babu kowa amma a cikin gidan" nace "ina Esther?" Yace "taje gida suna biki. Sai yau zata dawo" ssi kuma ya koma dakin sa da sauri ya dauko key ya kawo min. "ga keys ta bari da ma ko za'a yi bako" na karba nace '"'shikenan. Nagode Baba Ya'u". Na juya na shiga cikin gida amma ina jin sa yana kallo na. Na bude kofa na shiga, falon da duhu sai na kunna fitilar wayata da niyyar zan haska hanya ba sai na kunna fitilu ba. Ina haska fitilar sai ta sauka akan hoton Baba Hadiza da yayanta. Na karasa gaban su na tsaya ina kallon su, they all looked happy and kuma kamar ni suke kallo, Na saka hannu na shafa fuskar Ammie "hey Ammieme" sai kuma na wuce hoton na tafi hanyar da zan hau stairs zuwa dakina, Ina shiga dakin na kunna fitila, sai na ga Esther ta rufe komai na dakin da yadi dan kar yayi kura, atmosphere din dakin was suffocating tunda komai a rufe yake, na ajiye jakar hannuna na bude windows din akin sannan na yaye yadin da ta rufe gado da shi na bude closet na dauko bedsheet na zo na shimfida akan gadon sai kuma a shiga toilet nayo alwala na fito nayi sallah. Ina idarwa na mayar da windows din na rufe sannan na kunna ac na saka waya ta on silent mode na bi lafiyar gado na kwanta, and I slept like a baby, irin baccin da tun da naje gidan Mukhtar ban yi irin sa ba. Him👳🏻‍♀️ Three Months ago…… Kamar wani engine haka Muhammad Gidado ya mayar da kansa, daga ina kake aiki ina zaka je aiki me yi aiki, Abba da kansa had to tell him to slow down and take things easy. Within the first few weeks da ya fara yiwa abba aiki ya yi securing musu business deals da yawan da Abba bai yi tsammani ba. He takes risks and he no send anybody, Nan da nan sunan shi ya fara shiga bakunan business partners din su and they tried to make deals with him, wadansu deals din ya karba wadansu kuma yayi watsi da su, A gida kuma yana iyakacin kokarin sa na ganin cewa hanya bata hada su da Safina ba. Saboda idan bai ganta ba yakan manta da wasu abubuwan amma da zarar ya ganta zai ji duk damuwowin sa sun dawo masa sababbi fil. Sannan kuma babu yadda za'a yi su hadu din bata gaya masa maganar da zata tuna masa cewa ita yayar Safiyya ce and Safiyya is now someone else's wife. Wannan knowledge din kuma shine abinda yake fin komai dagula masa lissafi ya kuma bata masa rai. Idan kuma ran nasa ya baci sai yaje ya huce akan punching bag din da ya saka a cikin gym dinsa. Wannan punching bag din da ace mutum ce da babu kashin da ba zai karye a jikin ta ba saboda irin dukan da take sha a gurin Muhammad. A zuciyarsa yana son ya cigaba da digging labarin Safiyya kamar yadda ya fara, amma kuma yana dakatar da kansa dan yana gudun sabawa ubangiji, ya tabbatar Safiyya a yanzu matar aure ce tunda babanta da kansa ya gaya masa, cigaba da bibiyarta kuma a matsayin ta na matar aure haramun ne kuma zai iya jawo masa fushin ubangiji. A gefe daya kuma ya san the more he hold on to her the more soyayyar ta take karuwa a zuciyarsa wanda shima hakan ba dai dai bane ba kuma bai san inda hakan zai kai shi ba. Ya tuna da abinda tace masa, she said he should accept his fate kamar yadda ita ma tayi accepting kuma take facing na ta, ya tuna da tambayar da yayi mata akan tana nufin yayi accepting Safina? And she couldn't answer that, sai dai fuskar ta ta nuna tsantsar kishin sa da take yi akan Safina. Safinan kuma ita ce babban problem din sa a yanzu. Ya tsane ta. Ya tsane ta ba kadan ba. Ya kasa cire tunanin cewa tana da hannu a cikin koma menene ya samu Safiyya, koma menene ya chanja da Safiyya from a cheerful soul to a sorrowful soul. Gani yake yi kamar Safina ce tayi mata wani abu dan ta raba su ita ta same shi. Dan irin soyayyar da take nuna masa is scary, it is obsession. Ko kadan ©️? bata yin zuciya da shi ko tayi masa fushi duk kuwa da irin trailer trailer ta rashin mutunci da yake sauke mata. Sai dai tayi kuka ta gama ta cigaba da ga inda ta tsaya, Ko da sau daya bata taba fashin yi masa girki ba, zata yi breakfast ta kawo masa za kuma tayi dinner, ranar da taga yana gida bai fita ba har lunch take yi masa amma bai taba yin ko da loma daya ba. Sometimes he wondered me take yi da abincin idan bai ci ba? Shi kuma yana iyakacin kokarin sa wajan ajiye mata kudi a kusa da abincin da ta kawo din, a ganinsa ya rage wa kansa nauyin ta na ciyarwa. Amma kuma a kasan zuciyar sa ya san ba wannan ne kadai nauyin ta da yake kansa ba. But he couldn't even think of sauke dayan nauyin. God forbid…. Sai dai ita kuma a nata bangaren tana yin duk kan kokarin ta na taga cewa ya sauke wancan nauyin da yake gudu din, tunda ita lissafin ta shine sauke wancan nauyin shine kadai hanyar da zata bi ta ga ta juyo da hankalinsa gare ta. If only he will come to her bed……. If only he will let her go to his bed. Amma san babu hanya kuma babu fuska, Ta sha gwada shiga dakinsa, amma babu abinda take samu a cikin dakin sai wulakanci da bakar magana, Ta sha gwada yaudarar sa zuwa nata dakin, amma tun shigar da yayi ranar da su twins suka zo bai sake shiga ba. Sai ta chanja salo, har a falon nashi ba ta kyale shi ba duk inda yayi in dai yana gidan sai ta bishi ta nuna masa jikinta with any opportunity da ta samu. And then one day, three weeks after komawar su Safiyya Kano, about a month kenan da bikin su. Muhammad ya tashi da assuba yayi sallah sai ya shiga gym dinsa kamar kullum ya fara gudu akan treadmill, dama yanzu al'adar sa kenan kullum bayan sallar asuba zai shiga yayi exercise in ya gama kuma sai yaje yayi wanka yayi breakfast ya fita, exercise din yana sa ya zama more focused and more productive a gurin aikin sa. Kamar kullum ranar ma ya toshe kunnuwansa yana jin kida while running, his mind focused on the lyrics. A lokacin ne yaji kamshin turarenta and yaji haushin kansa for forgetting to close the door. Dan yanzu ya zama shi da gidan sa amma bashi da ikon barin kofa a bude sai ta shigo ta takura masa, Ya cigaba da abinda yake yi, knowing fully well abinda zai gani dan ya kalli inda take and he wasn't looking forward to it. Amma bata hakura ba sai da ta taho ta zagaya ta tsaya a gaban treadmill din. Wando ne a jikin ta three quaters length wanda ya kama ta sosai dan Muhammad ya tabbatar sai da ta sha wahala kafin ta saka shi, da kuma half vest wadda ko rabin cikinta bata rufe ba kuma babu brazier a cikin ta. Tayi packing gashin kanta a gefe daya ta zubo shi kan kafadar ta daya, fuskar ta babu kwalliya sai murmushi da yake kwance a lebenta. Yayi sauri ya sauka daga kan treadmill din dan saura kadan ya fadi "damn it" ya fada cikin tsawa tare da dafe kansa "what the hell are you doing here?" Tayi magana amma bai ji ba saboda kunnensa da yake toshe. Ya cire abin kidan sannan ya sake cewa cikin tsawa trying as much as he can to not look at her "Malama ki fita ki bani guri, Wai ke wacce irin mutum ce? Are you insane? Haka aka koya miki tarbiyya a gidan ku?". Ta saka hannun ta daya tana shafa gashin kanta zuwa kafadar ta tace "gidan mu sunyi min tarbiyya sosai, Na kuma gode musu. Ban ga abin rashin tarbiyya dan na gaishe da miji na ba, Ina fatan ka tashi lafiya" yace "to be frank with you, lafiya lau na tashi and I was looking forward to this day saboda ina da muhimman abubuwan da nake da su a gaba na, but now I am not so sure. You destroyed my morning with your presence. Now get out of my site". Amma maimakon ya ga bacin ran abinda ya fada a fuskarta sai yaga murmushi ta cigaba da yi. "I am sorry Habibi. Na san ma bata maka morning dinka tunda yanzu na tabbatar in kaje office babu abinda zaka iya yi sai tunani na. And that's exactly what I want. I want you to think about me, and know that I am yours, and I am here a cikin gidan ka a matsayin matar ka and …. ..." Ya nuna mata hanya "ki fita nace miki tun kafin in chanja miki kamannin ki. You have no idea how much I have been trying to control my temper around you. Ki kwashe wadannan kafafuwan na ki ki dauki sauran mutuncin da ya rage miki ki fita. You have no idea how much I hate the site of you" amma maimakon ta fita din kamar yadda ya bukata sai ta durkusa a gaban sa fuskar ta a kasa, "Muhammad. You can hate me all you want, amma kasan cewa ni ina son ka. Bana jin akwai wata mace kaf duniya da zata yi maka irin son da nake yi maka, Kuma...... ."Bai jira sauran maganar ta ta ba ya juya ya fice ya bar mata gym din, yana shiga dakin sa ya mayar da kofa ya rufe dan gani yake yi zata iya biyo shi nan din ma. Bayna ya rufe kofa sai da ya jingina kansa a jikin kofar tare da rude idonsa yana mayar da numfashi, wannan wanne irin tashin hankali ne .... Yarinyar nan ta wuce duk inda yake tunani a rashin aji. Abinda kuma ya tabbatar wa kansa shine ba zata hakura ba. Dan da zata hakura da tuni ta hakura. Da tana da zuciya da tuni tana gidan su. A ranar a office ya yanke wata shawara. Kasar zai bari. Akwai wasu tafiye tafiye dama da ya fara tunani akai amma kuma bai yanke shawara ba, wadansu tarurruka ne na oil marketers da za'ayi a kasashe uku cikin watanni uku masu zuwa, kowanne wata daya za'a yi taro daya a kasa daya, he was thinking of going to one of the countries, amma ranar kawai sai ya dauko takardu ya cike duk kasashe ukun. Yana bukatar hutu gaskiya. Yana bukatar time away from everything and everyone musamman wanna halittar da take gidan sa. A ranar ya fara processing tafiyar, yadda ya tsara shine in ya tafi ba zai dawo ba sai an gama dukkan tarukan, daga kasar farko zai wuce ta biyu sannan kuma ya wuce da uku. Ana tashi daga office ya tafi gida ya fara yiwa Abba bayani, Abba ya fahimta sosai kuma yaji dadin yadda yake kokarin gain cigaban business din su. Amma kuma sai ace "amma da matar ka zaka tafi" Gidado yaji kamar Abba ya kwada masa mari, yace "Abba business trip ne fa? Ta yaya zan ringa yawo da ita a cikin mutane? Ita kanta ba zata ji dadin tafiyar ba" Abba yace "zata ji dadi mana. And who told you ba zaka iya zuwa da matarka business meetings ba? She is your wife, you can take her anywhere. Muhammad ya dafe kai yana jin kamar zaiyi kuka. Sai bayan da Abba ya tashi sannan Mama ta dawo kusa da Muhammad tace "you want to run away from your responsibilities ko?" Ya gyara zaman sa yace "haba Mama, wanne run away kuma sai kace wani yaro. I just want a little peace" tace "tana vi maka wani abu ne a gidan that is not peaceful?" Yayi shiru bai ce komai ba, bai sani ba ko tsayawa a gabansa almost naked can be counted as "not peaceful" ta cigaba "ni ina ganin ka dauke ta ku tafin Muhammad, you both need the trip, Maybe tafiyar zata yi clearing issues din ku ta samar muku fahimtar junan da kuke lacking" yace "Mama. I planned the trip to get away from her. How can I then carry her along on a trip that is meant to get me away from her" Mama tayi shiru tana kallon sa, daga alama bata gane ba, shima kan sa bashi da tabbacin yana making sense or not. O Ganin duk ba zasu fahimce shi ba sai ya mike zaiyi mata sallama ya tafi. Tana ta kallon sa tace "you are still thinking about that girl ko?" Ya tsaya bai ce komai ba kuma bai juyo ba, tace "wannan abin da kake yi kana tayar da hankalin ka kaki ka kwantar da hankalin ka kayi concentrating on what God has blessed you with duk saboda Safiyya ne ko?" Ya juyo yana kallon ta amma bai ce komai ba, he can see the hurt on her face amma kuma ba zai iya ce mata ba saboda Safiyya bane ba saboda shi ya san saboda itan ne. Bai koma gida direct ba, sai da yayi yawo a gari a mota dan ya danyi clearing brain dinsa ya kuma nemawa kansa mafita. Yana jin haushin kansa for loving Safiyya too much, yana jin haushin Safiyya for making him go through this dan a ganinsa ita tayi causing komai, Sai da dare yayi sosai sannan ya dauki hanyar gida, Sai dai kuma to add to his troubles yana zuwa kofar dakin sa ya saka key zai bude sai yaga kofar ta bude, and he saw her standing a tsakiyar dakin tana jera pillows akan gado. Ya fahimci kamar ta chanja beddings din ne. Ya tsaya yana kallon ta, ta gama jeran pillows, ta dauke wannan ta juya wancan tayi straightening wannan har ta gama sannan ta dauko turare tana fesawa akan gadon. Ya na daga bakin kofa yace "cire su ki mayar da su inda kika debo su" ta juyo tana kallon sa, daga alama ba ta san da zuwan sa ba. Ta dan yi murmushi "yayi kyau ko?" Bai ce komai ba ya sake hade rai. Ta cigaba da murmushi "yayi min kyau sosai, saboda na ka ne" ya sake maimaita abinda yace "ki kwashe min su daga kan gado ki mayar da su inda kika debo su". Bata yi hakan ba sai ta tako ta taho inda yake tsaye, rigar bacci ce a jikinta with a very low neckline da yake bayyanar da kusan rabin kirjinta. Ta tsaya a gaban sa suna kallon juna. "get out" ya fada cikin muryar da take nuna tsananin tsanar ta. Tace "Muhammad. Dan Allah ka tsaya muyi magana ko da sau daya ne. Ka bani da ma at least kaji abinda yake zuciya ta" ya saka hannayensa a aljihunsa yace "okay, Menene a zuciyar taki, That is in kina da zuciyar kenan" ta langwabe kai tace '"babu mutumin da Allah yake halitta babu zuciya a kirjin sa, kamar yadda Allah yake rubutawa kowa kaddarar sa, ni tawa kaddarar ita ce soyayyar ka" yace "wrong answer. The only words I want out of you is a confession. Ki gaya min yadda kika saci saurayin kanwarki, and yadda kika yi crawling into my life" ya girgiza kanta "wallah ban san kai saurayin ta bane ba. Ban san sau nawa zan rantse maka akan hakan ba. Bani da hannu sam akan rabuwar ku. I only know ina son ka. Soyayyar ka ita kadai ce abinda na sani a cikin duk wannan maganar. And I will do anything for you. Duk abinda kace inyi maka wallahi zanyi maka indai bai sabawa ubangiji ba. Saboda ina son ka. Ina sonka sosai Muhammad". "Get out" ya sake fada, tayi kamar zata yi kuka "please Muhammad ko yaya ne ka yarda da ni mana. You have no idea how I am hurting akan abinda kake yi min. o da ba zaka so ni yanzu ba ka bani dama in nuna maka tawa soyayyar. Na tabbatar maka wata rana you will look back and thank God for separating you from Safiyya and giving you me" Ya ja kofar akin da hannunsa daya yace "how dumb are you? Menene baki gane ba wai? Get din ko kuma out din? I said get out" har tazo zata wuce shi kuma sai yace "wait" ta dakata with hope a fuskar ta sai ya nuna gyaran gadon da tayi yace "take your trash out with you", Haka ta koma ta nannade duk shimfidar da tayi ta rungumo kayanta a hannun ta tazo zata wuce shi, sai a lokacin yaga hawayen da yake bin fuskarta, ta tsaya a bakin kofa tace "kamar kullum dai. I am sure you will come around one day. Akwai anar da zaka fahimci banbancin soyayyar karya da ta gaskiya, and when that day comes, I will be here to wipe away your tears". Washegari ya cigaba da shire shiryen tafiyar sa, the first meeting is in a weeks time, wannan ya bashi idea din yadda zai yi ditching Safina ya ki tafiya da ita kamar yadda iyayensa suke so. "She doesn't have a visa, da kyar na samu tawa nima, amma zan cigaba da processing tata from there, I have someone da yake harkar visa din nan. He will help", Farko Abba yaki y yarda da shi amma da ya yi masa bayani a nutse na cewa sunansa ne kawai akan invite din meeting din, sannan kuma tunda ba ta amfani da sunansa dan haka it is hard to convince them cewa matarsa ce, Daga baya dai Abban ya yarda, amma Mama ta san yana sane, sai dai kawai tayi shiru ta rabu da shi. And then two days to ranar tafiyar ta sa, ya dawo gida da daddare kamar kullum, ya shiga part din sa ya rufe kofa, ya kalli kan dining table dinsa ya ga abinci kamar kullum, ya karasa ya tsaya yana kallon abincin and he saw a note a kusa da plates din da ta jera "for all the hurtful words you said to me, na yafe maka tun kafin ka nemi yafiyar because I love you, dan Allah yau dai kadai kaci abincina" ya bude yaga tuwon shinkafa ne miyar taushe. Ya mayar ya rufe sannan ya jona electric jug din da yake dafa tea a ciki ya shiga daki ya fara shirye-shiryen sa. A ranar yake so ya hada kayansa, ya koma dining ya zubo tea din sa ya dawo dakin yana aiki yana shan kayansa har ya gama, ya zuba kudi masu dan yawa a envelope ya ajiye da niyyar ranar da zai tafi zai ajiyewa Safina with a note saying in ta gaji da zama ta tafi gida. Yana gamawa yayi wanka yayi shirin bacci ya kwanta, Sai dai me? Baccin ne ya gagare shi, Wani irin yanayi yake ji da bai taba jin irin sa ba, Farko ya dauka zazzabi ne zai kama shi dan yadda jikinsa ya dauki zafi gabaki daya, amma kuma maimakon sanyin da ake ji in ana zazzabi shi zafi yake ji, wani irin zafi kamar babu iska a dakin, ya tashi da niyyar karo karfin ac amma sai yaji marar sa tayi wani irin daurewa, ji yayi kamar jinin jikinsa gabakidaya ya tattara ya dawo marar sa ya tare. Kanshi yayi nauyi sosai yana sara masa kamar zai tsage. Ya kwanta ya lulluba da bargo sai kuma ya yaye bargon, ya cire rigar jikinsa ya ajiye amma still zafi yake ji. Da kyar ya tashi ya shiga toilet ya sakar wa kansa ruwan sanyi, ya jima yana jin dadin saukar ruwan sanyin a jikin sa sannan ya fito ya koma ya kwanta ba tare da ko ruwan jikin sa ya goge ba. A haka bacci mai nauyi ya dauke shi. Cikin baccin yaji motsi kamar an shigo dakin sa, ya tashi da sauri yana jin ciwon kan yana sake dawowa, a dai dai lokacin da Safina ta fito daga toilet dinsa jikinta daure da karamin towel din sa, kamar daga wanka ta fito. Cikin takaici da mamaki yace "what? What the hell are you doing here?" Tayi pretending kamar ta tsorata ta yar da towel din jikin ta, sai kuma ta sunkuya ta dauka ta mayar ta daura "am sorry Habibi na baka toro, zafi nake ji kuma shower din toilet dina ta lalace" bai iya ce mata komai ba har ta fita. Ya koma ya kwanta rigingine yana kallon rufin dakin, kusan five minutes yana a haka sannan ya mike and went straight to part dinta straight to her room, kofar a bude take fitila ma kuma a kunne, tana kwance akan gadon ta wearing silky doguwar rigar bacci with nothing inside. He went in an switched off the light. Sanda ya fito daga dakin he banged the door with so much anger kamar zai karya kofar, bai kuma koma bacci ba instead sai ya tafi gym dinsa and punched the living light out of his punching bag. Ji yake yi ya tsani kansa, ya tsani Safina ya tsani kowa including Safiyya. Washegari da safe, for the first time in history na auren su Safina bata kawo masa breakfast ba but ko kallon inda dakinta yake bai yi ba. Ya san ya kamata ya duba ta, a matsayin sa na mijinta especially after what happened between then the night before, amma bai je ba ya tafi office dinsa, sai da ranar aikin gagarar sa yayi, a duk iyakacin kokarin sa na ganin ya cire abinda ya faru tsakanin sa da Safina da daddare amma ya kasa ¡ya cirewa, A karshe sai ya tattara takardun sa yayi. wa mutanen sa sallama akan cewa tafiyar da zaiyi ce ta saka zai tashi da wuri dan yaje ya kammala shire shirye. Sai dai yana zuwa gida part dinta ya dosa, bata falo and he went straight to her room, yana shiga ya tarar da ita ta fito daga wanka, kallo daya tayi masa ta san abinda ya kawo shi, sai da kayan cikin ta suka kada saboda toro dan a lokacin ma da kyar take daga kafarta. Amma sai ta kirkiro murmushi, a gurin ta wanna wata babbar nasara ce, maybe he will appreciate her now. But after he did what he came to do, buga mata kofar da yayi yafi na daren jiya ma karfi. Ta koma ta kwanta tana jin hawaye yana bin fuskarta. He is everything she had hoped and more, but this is nothing she had imagined. Instead of love and passion, what he gave her was anger and hate. She expected hugs, kisses, smiles and snuggles with a little touch of passionate words. But she did not get any. And when she draged her self out of her room sai ta ga envelope a kuss da tvn ta, with a handwritten note. "Forget about what happened, Nayi tafiya. If you cannot stay you can go" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Three : Plan C A ranar bai kwana a gidan ba sai ya tafi daya gidan sa ya kwana a can. Ko kuma muce ya kwanta a can. Dan baccin gagarar idanunsa yayi. Shi ya san abinda yayi ba laifi ya aikata ba but at the same time it felt so wrong. Ya san ya bude wani fejin da bai san yadda zai yi ya rufe shi ba. He thought he had everything under control zai cigaba da keeping Safina a gidan sa har zuwa lokacin da zai samu hujjar da zai gabatarwa da iyayensa yadda zasu amince masa ya sallameta, ko kuma ita zata gaji ta nemi sallama, shi kenan komai zai kare with no strings attached. But now he have attached the strings. Amma shi kansa bai san ta yadda ya kulla wannan zaren ba. Ta yaya? How? Why? Kwata kwata ba zai iya bayanin ya akayi hakan ta faru ba. Shi dai yasan yana da lafiya a wannan bangaren, sosai, bai taba vi ba but he have all the feelings na mazantaka toward wacce yayi burin bude wannan babin da ita, wanna yana daya daga cikin dalilan sa na matsa mata akan maganar aure, but then one thing lead to another and he found himself married to Safina. And he lost all the feelings, especially idan ya tuno da dangantakar ta da Safiyya ko kuma idan tayi kokarin yi masa tallan jikin ta. It disgust him. Rashin class dinta yana daga cikin abinda ya saka baya kallon ta a mace. The more da take zubar da ajinta a gurin sa the less yake mata kallon mace. Shi yaso ace idan zai samu wannan abin sai ya nema sannan a bashi da kyar bayan an gama ja masa aji. But that doesn't change the fact that shi namiji ne ita kuma mace, and dole yana da bodily urges wadanda yake kokari wajan keeping on check. His desires have always been under control and he was so sure of himself yana ganin ba gida daya ba ko daki daya ne zai iya kwana da matar da baya so kuma ya tashi ba tare da yaji ko gezau ba. But what happened yesterday wasn't normal. It wasn't natural. He had never felt anything like that before in his entire life, bai kuma taba tunanin akwai wani abu irin wannan ba. It was scary, And totally disappointing at the end. Desire din was huge but the satisfaction was close to zero, wannan shi ya saka shi yayi wanting more but the more was even more disappointing. Ba zai iya kwatanta abin ba, kamar karin maganar da Hausawa suke cewa ga koshi ga kwanan yunwa. Shi dai yasan dole akwai abinda yarinyar nan ta yi mishi, yafi kuma tunanin cewa asiri ne dan irin yadda take naci akan sa tabbas zata iya yi masa asiri dan ta same shi. Duk da dai ya san shi baya wasa da addu'a, amma kuma asiri babu wanda ba zai iya kamawa ba. Abinda ya faru dai ya riga ya faru, yanzu saura ya san menene zaiyi akan hakan. Shin wannan abin da ya faru yana nufin ya karbi auren sa da Safina kenan? But just the thought gave him shivers, ba zai iya imagining spending his entire life with Safina as his life partner ba. Amma kuma in ya sake ta babu laifin tsaye babu na zaune even after what happened anya Allah ba zai saka mata ba? Especially if she is saying the truth about not having a hand in rabuwar su da Safiyya. But all that decisions will come after ya gano what happened with him the other night, idan har da gaske wan abun tayi masa unnatural then ya tabbatar babu abinda ba zata iya ba kenan. Wannan kuma zai kara masa tsanar ta and may lead to their separation. Washegari ya je gida yayi wa mahaifansa sallama sannan Haidar ya kaishi airport ya tafi. And it has been over two months now da tafiyar sa. Sau daya bai taba daga wayarsa ya kira Safina ba. Tayi kiran har ta gaji baya dauka. She sent him messages zai karanta yay ignoring. She sent him voice notes, sometimes crying and expressing herself amma kamar da dutse take. Abinda ya fahimta shine kamar after what happened between them her obsession with him increased. In one of her vns ne ta gaya masa cewa bata da lafiya and she thinks she is going to die. Daga nan ya daina sauraran vn din ko ta turo, ya fahimci tana son tayi gaslighting dinsa to make him feel guilty. Yana aika Haidar ya kai mata kayan abincin duk da ake bukata a gida, ya kuma bata kudin kashewa. On the other hand kuma ya mayar da hankalinsa sosai kan abinda ya kai shi. Sanda yayi watanni biyu a can ne Mama ta kira shi tana yi masa fadan wai ashe Safina bata da lafiya amma duk wayar da suke yi kullum bai taba gaya mata ba, ta ce sai a bakin Mommyn safinan ta ji a gidan biki. Sai kuma ta fara zancen zata tafi da Safina gurin ta ta zauna tare da ita har lokacin da zai dawo. Dama tana ta kewar Mufida. Wannan maganar ba ta yi masa dadi ba, shi gani yake ciwon munafunci ne Safina take yi dan ta ja hankalin sa da na iyayensa kanta, yanzu gashi tayi nasarar jan hankalin Mama kuma bai san irin kissar da zata vi wa maman ba a zaman da zasu yi tare kafin ya dawo. Wannan ya sa ya fara rounding things up dan ya samu ya dawo din amma abubuwa suka ki yin sauri. Kullum a ransa tunanin Mama da Safina yake yi together, kar taje ta gaya mata wata maganar, kar taje tayi mata wani abun. Still har Safina tayi sati biyu a gidan su bai samu dawowa ba. Her🧕🏻 Ban san awa nawa na dauka ina yin wannan baccin ba. Sanda na farka daga yanayin hasken gari na fahimci cewa rana tayi sosai. Na jawo waya ta da take gefena na duba lokaci 1:30pm. Na tashi zaune tare da jera adduoin tashi daga bacci sannan na sake daukan wayar tawa na duba naga several miss calls, wadansu daga grin Daddy wasu kuma daga gurin Uncle Ahmad. Nayi ajiyar zuciya. This is going to be a very long short day for me. Na koma na kwamta rigingine ina kallon saman dakin, thinking, saboda nayi bacci mai nauyi sai naji kwakwalwa ta ta ware sosai and every thing looks clear to me. Na gama planning din abinda zanyi. Babban matsala ta shine Daddy, bana son ransa ya baci ko kadan kuma na san dole ran nasa zai baci, I wasn't looking forward to breaking the news to him dan na tabbatar it will break him down. Yes, baya son Mukhtar amma kuma Mukhtar dan dan uwansa ne. Kuma babban abinda zai kara masa damuwa in all this shine the fact that bai yarda da ni ba when I told him I was raped, in fact har yau bai yarda cewa I was raped din ba. Na tashi zaune ina murmushin jin dadin halin da na bar Mukhtar a ciki. Na san zuwa yanzu jikinsa yayi tsami ba kadan ba, amma kuma na sam duk tsamin da zai yi ba zai kai yadda nawa yayi a lokacin da ya aikata min abinda ya aikata min ba. Sai dai kuma nay mamakin kiran uncle Ahmad da na Daddy da na gani. Kar dai ace har sunje gidan sin ganshi? Ba zanji dadi ba idan haka ta kasance saboda ina sane na barshi yayi hours a daure dan ya dandana yaji, kuma ina son in zama wadda zata yi breaking news din to them. Na lalubo number din Yaya a waya ta duk da yadda the nutty part of me yana zuga ni in kira Umma ko Abba. Na yi dialing number din bai jima ba ya dauka "hello Fiyya, ina kuka shiga ne ke da mijin ki?" Ban amsa tambayar ta sa ba nace "kana i ina ne?" Dan naji kamar a hanya yake, yace "ina hanyar gidan ku. Abba ne yace inje in duba ku wai ana ta kiran wayoyin ku ba'a samu" nace "alright. Shikenan ma. Da ma zance maka kaje gidan ne gurin Mukhtar. Ni bana nan naje gida. In kaje don't bother knocking kawai ka shiga" daga nan na katse kiran dan nasan tambayoyi ne zasu biyo baya. Daga nan sai na kira Daddy, shima tana shiga ya dauka and his sick voice sounds worried "Safiyya? Ina kika shiga? Malam Ya'u ya kira ni tun da zu yace wai kinzo gida da asuba, Kuma nayi ta kiran wayoyin ku ke da Mukhtar baku dauka ba. Allah ya sa dai lafiya kike" na sassauta murya ta sosai "Daddy lafiya lau nake, kar ka damu da ni" yace "damuwa kam ta zama dole Safiyya, as parents it is our job to worry about our children. Musamman make. Me kike yi a gida? Me yasa kika fita daga gidan mijinki da assuba? Da wani abun ya same ki fa? Ko fada kuka yi?" Na yi shiru ina jujjuya maganganun a raina, bana son gaya masa a waya dan bansan yadda zai yi reacting ba, bani da tabbas din kuma akwai wani a tare da shi. Nafi son muyi magana face to face da shi yadda zanfi iya controlling emotions din sa nace "Daddy lafiya ta kalau. Kuma ina gida kamar yadda Baba Ya'u ya gaya maka. Ka tuna abinda nace maka ranar da zan bar Kano? Nace maka everything will be okay? To akan maganar ne, things are beginning to be okay. In anjima kadan uncle Ahmad zai kira ka, Please Daddy duk abinda zai gaya maka kar ka tayar da hankalin ka, kamar yadda na gaya maka I am okay kuma I am safe a gida. Zamuyi maganar as soon as I come to Kano" Ya yi shiru, farko na dauka ma kiran ya katse sai kuma naji yace "kar ki fita daga gidan, I will be on the next flight to Abuja". Sai ya katse kiran, Na ajiye wayar tare da dafe kaina, Kamar yadda ya fada haka ne it is parent's job to worry about their children, but I don't want him worrying about me, especially in his condition. Amma kuma na san a karshe idan aka gama maganar ya fahimci komai damuwarsa zata ragu sosai zai ji dadi sosai dan zai gane cewa ban aikata abinda yake tunanin na aikata ba, zai kuma kara fahimtar cewa I am capable of taking care of myself ko da bayan baya duniya. Na tashi na shiga wanka, ina wankan ina jin waya ta tana ta kara amma I took my time nayi wankana a nutse dan na san ba Daddy bane ba, na fito na shirya nayi sallah sannan na bude dakin na sauka kasa, ina sauka naga Esther, ta taho gurina da sauri tana gaishe ni tare da bani hakurin rashin samunta da banyi ba a gida, I smiled at her and asked her to get me something to eat, bata jima ba ta dawo, daga alamu ta yi dama already tun kafin in tashi. Na zauna a kasan hoton Ammi naci abinci nana koshi, sannan na kuma dauko waya tana duba, missed calls from Yaya, uncle Ahmad da kuma shugaban marasa kunyar duniya, Mukhtar, Banyi returning kowanne call ba na kunna tv na cigaba da zama na a falo yayin da Esther take aikin gyara min dakina. Har la'asar sannan na tashi na koma saman na tarar da gyara komai dakin sai kamshi yake yi. Navi sallah na sake fitowa na tarar har ta gama lunch tana jerawa a dining. Nayi mata sannu sai ta ce min ai Mommy ta kira ta a waya tace gasu nan zasu taho. Na koma na zauna kawai ina kallon hoton Ammie, wato har yanzu Mommy bata huce da ni ba tunda bata kira ni ba sai ta kira Esther. Ina da zaune a gurin sai ga kiran Mustapha, na dauki wayar ina kallon number din sa, yaushe rabon da muyi waya da Mustapha? Bazan iya tunawa ba. Na dauka na saka a kunne na "Fiyya Daddy yace kar ki ce zaki zo daukan mu, zamu taho da motar airport" "to" kawai nace masa na ajiye wayar ina jin wani iri a raina. He sounded just like the voice that called me that day. Shin da bakin sa a cikin maganar nan ko kuma he is innocent framing dinsa Mukhtar yayi? Tun yarintar mu na san Mukhtar da Mustapha ba sa shiri, in dai suka hadu sai sunyi fada kuma lokuta da dama a kaina ne suke yin fadan dan Mukhtar ya fahimci cin zalina da Mustapha yake yi shi kuma tunda ya fi shi karfi sai ya rama min, daga baya bayan sun girma sai suka dore a haka, not just about me basa jituwa sam, they disagree on everything. Bana jin zasu samu agreement on raping me, it iust doesn't make sense. musamman yadda a dai dai lokacin da abin ya faru Mustapha da Mukhtar sun cikin heated rivalry akan son aure na. Nayi ajjiyar zuciya tare da ture tunanin da ga zuciyata, ko ma menene Mukhtar zaiyi bayani da bakin sa dalla dalla. Ina nan dai zaune naji an bude gate sannan naji tsayuwar mota. Na mike tsaye ina kallon kofar. Mustapha ne ya fara shigowa, ya tsaya yana kallona kamar yadda nima nake kallon sa, kamar zai ce wani abu sai kuma ya juya ya koma da sauri. Yana fita Mommy ta shigo, sannan Mustapha ya sake dawowa tare da Daddy. Gabakidayan su yanayin su ya nuna cewa suna cikin damuwa. Mommy ce ta fara magana "Safiyya me ya same kike kuwa? Da gaske ne abinda Ahmad ya gaya mana wai kin tozarta mijinki irin haka? Ki tube mutum tsirara ki daure shi akan gado? Mijin ki fa Safiyya?" Muka hada ido da Mustapha and I saw yadda yake kokarin hana kansa dariya, nayi kamar ban ganshi ba na fara kokarin yiwa Daddy magana "Daddy sannu da zuwa" ya juya kujerar sa zuwa hanyar part dinsa ace "zamuyi magana in an jima, Sa'adatu kar ki tayar da maganar nan", Mommy ta bishi da kallo sai da ta tabbatar ba zai ji ta ba sannan tace "yaya zanyi kuwa ba zan tayar da magana ba. Ni na san da akwai wata a kasa kuma dole in bincika inj'" ta juyo kaina" Me yayi miki? Yanzu muma sauka naji Ahmad yana yi masa waya wai ga abinda kika yi wa mijin ki, kaninsa yaya ne yaje ya ganshi a hakan ya kira iyayen. Gaya min inji me yayi miki". Uncle Ahmad ne ya shigo falon kamar an jefo shi. Yana shigowa muka hada ido and he gave me just the look that I expected him to give me sannan ya fara magana "ina Yaya? Ina bukatar ganin sa yanzu yanzun nan?" Babu wanda ya amsa masa sai yayi hanyar shiga part din Daddy, Mommy ta daga murya "dakata dakata, yace kar wanda ya shiga gurin sa tukunna. Yanzu muka sauka hutawa zai yi sai anjima za'a yi maganar" ya juyo a fusace yana nuna ta da yatsa "ke Sa'adatu ki fita daga ido na. Ke kin isa zan ga danuwana ki gaya min yaushe zan ganshi ko yaushe ne ba zan ganshi ba?" Kafin tayi magana Mustapha ya tsaya a gabanta yana kallon Uncle Ahmad yace "sauke wannan hannun da ka daga" Uncle Ahmad ya saki baki da mamaki, daga alama bai taba tsammanin haka daga Mustapha ba yace "ni kake kallo cikin ido kake cewa in sauke hannun na?" Mustapha yace "exactly. Kana mamaki ne?" Uncle Ahmad yace "idan ban sauke ba kuma fa? Me zai faru?" Mustapha yace "sauke maka shi zanyi kawai. Shine abinda zai faru" Uncle Ahmad yace "lallai yaron nan ka cika marar kunya. Ni lake gaya wa magana irin haka? To wallahi kasan ina da yayan da da hannu daya zasu iya karya min kai kamar rake" Mommy ta fara jan Mustapha "rabu dashi Mustapha. Neman wanda zai huce a kansa ya ke yi kar ya huce a kanka" Uncle Ahmad ya taba kofar Daddy yaji a rufe sai kuma ya dawo yazo inda nake ya nuna ni da hannu "ke kuma!" Sai kuma ya girgiza kansa "ban ma san me zance miki ba. Kin bani mamaki" daga haka sai ya juya ya fita. Mommy ma tazo ta wuce ni ta hau sama tana cigaba da mita "haka kawai. Zaka 20 kana mana hayaniya a ka. A bari mana a tambayi yaran aji menene ya hada su?" Ni dai na koma na zauna tare da rufe idona. It has started. Ban san kuma yaushe zata yi ending ba, Ina bude ido na muka hada ido da Mustapha, yana tsaye a jikin kofa yana kallona. Na mike na dauki jaka ta zan hau sama sai ya kira sunana "Fiyya" na tsaya amma ban juyo ba sai yace "da gaske ne abinda aka ce kin yi masa? Da gaske ne kin rubuta masa "RAPIST " a goshinsa?" Na juyo ina kallon sa sai ya daga kafada yace "haka naji Daddy da uncle Ahmad suna fada a waya" ya dawo da baya ina kallon sa nace "menene naka a ciki? Huhh? what do you want?" Ya gyara tsayuwa "nothing.….…..kawai dai kin san ni yayan ki ne and I care about you duk da kiyayyar da kike yi min. I know we have had our share of problems a tsakanin mu. Ki gaya min abinda yayi miki, kin san Daddy yanzu cewa zai yi kiyi hakuri, ni kuma in kika gaya min nayi miki alkawarin zan dan farfasa masa baki ko hakora uku ne in ciro in kawo miki. Maybe to make up for my mistakes" na nuna shi "nothing will make up for your mistakes" ya daga kafada "okay okay, don't shout. Naji. Allah ya gani ina kokarin ganin mun daidai ta ke kuma kin ki. Any time you need me just call me" ya juya zsi fita, Har ya kai bakin kofa sai kuma wani tunani yazo min and I called his name "Yaya Mustapha" ya juyo and I saw a smile on his face, na taka zuwa gabansa na tsaya muna kallon juna nace "I want to ask you something. Ansar da zaka bani kuma zata yi matukar tasiri gurin gyaran tsakanin mu. Ranar da kuka dawo daga Cyprus kai da Daddy, ranar da ka yi min sharri kace ina yin shaye shaye, ka kira ni a waya kace in zo Daddy bashi da lafiya?" Ya dan bata fuska yana kallona yace "kamar kin taba yi min wannan tambayar, ko kuma Daddy ne? Ni ban kira ki a waya ba, ta yaya zan kira ki a waya alhalin ina cikin jirgi tare da Daddy?" Na gyada kai na "are you sure? This is very important" yace "I am sure. Menene wai?" Na koma da baya na zauna akan kujera nace "kasan wata hanyar da za'a iya bi a kwaikwayi muryar mutum a waya?" Ya dawo tsakiyar falon ya a kallo na yace "technology yanzu babu inda bai je ba Fiyya. Ba murya ba har kamannin mutum ana iya cloning, why are you asking this questions" na dora kafa daya akan daya nace "on the 13th of sep last year, around karfe takwas na dare, someone called me with a new number and called himself Mustapha, ya kuma yi magana da irin muryar ka sak, da na fito he attacked me, drugged me, kidnapped me and •......... Nayi shiru ido na yana kallon sa ban karasa ba, ya sauke rungumar da yayi wa hannayen sa fuskarsa tana nuna fahimtar magana ta, ya karasa min "and raped you" na gyada masa kai ina jin hawaye yana zuwa ido na. Yayi shiru yana kallon hawayen ido na daga gani one and one yake hadawa a kansa and I saw sanda labarin ya gama haduwa a cikin kwakwalwar sa "that bastard!" Ya fada da dan karfi. Nayi sauri na mike kar ya hada min mutane, ya cigaba "it was Mukhtar. That bastard. Shine and he tried to frame me. He used my name and my voice saboda ya san bama shiri dan kiyi zargi na. He knows Daddy bashi da lafiya he probably knows ranar zamu zo gari. He raped you and framed me. Wallahi sai naci kan bu** ub* sa" yayi hanyar waje da sauri ni kuma na bishi na jawo rigarsa tare da tare hanya. "me kike yi haka? You still want to defend him?" Nace "no.... Babu abinda nake bukata yanzu irin justice for what he did to me. Za su zo in an jima. will have my Justice then you can do whatever you want with him. Kar kaje yanzu kayi masa illar da zata bashi damar playing the victim card. Let me finish with him first then you can have him". Yayi shiru yana kallona, sai kuma ya gyada kai, Fuskarsa tana nuna tsananin bacin rai. Na matsa na bashi hanya ya wuce sannan nima na koma dakina, Ina dakina har aka yi sallar magrib nayi sallah sannan na cigaba da zama ina kallon agogo. A lokacin kiran Mukhtar ya sake shigowa cikin waya ta, na bishi da kallo har ya katse wani kiran ya sake shigowa, a haka har ya kira sau biyar sai kuma ya tiro min message "please Safiyya, we can still fix this. Kar muyi wannan maganar a gaban iyayen mu. I still love you with all my heart dan Allah" na karanta na mayar na ajiye wayar. Har na fara fitar da ran za'a zo kirana sai ga kiran Mommy ya shigo wayata. Na daga na saka a kunne na sai tace "ki zo muna falon Daddy" na tashi dama da hijab din da nayi sallah da shi a jiki na na dauki jakata making sure abinda nake bukata yana ciki sannan na fita daga dakin. Ina shiga falon na gansu gabakidayan su a zazzaune. Daddy, uncle Ahmad, Mommy da kuma Umma. Sai Mukhtar a kasa a kusa da kafafuwan Umma, ya dago kai ya kalle ni sannan ya dauke kansa. Nayi sallama na shiga na zauna nima a kasa kusa da Mommy, Ban gaishe da kowa ba, Shiru babu wanda yace komai na dan wani lokaci sai kuma Umma ta fara magana "wannan wanne irin wulakanci ne? Babu yadda da ma banyi ba akan kar ayi auren nan amma aka nuna min ni bare ce wai za'a rufa wa yan uwa asiri, gashi nan kum rufa mata asirin ita kuma ta bankada muku naku a duniya. Dama ba sa'ar auren sa bace ba. Tafi shi kudi ta fishi budewar ido da wayewar duniya. Babu bangaren da idanun ta basu bude akai ba. Yanzu gashi ." Mommy tace "yanzu gashi magana ta dawo baya. Tunda ta kira shi da rapist kuwa ai magana ta dawo baya. Yanzu ba mu da tabbas din wanda aka rufawa asiri da wanda kuma ya rufa wa wani asiri. Sai mu tsaya mu saurare ta muji abinda ya saka ta gaya masa haka....". Daddy yayi gyaran murya "zaku tsaya muyi magana ne ko kuma ku zaku vi maganar? Idan ba zaku yi shiru ba ku fita" na daga kai jna kallon sa and he looked older than I knew, kamar shekaru sun karar masa akan wadanda yake da su. Sai naji banji dadin putting him through wannan ordeal din ba amma kuma dole ce ta kawo hakan. Ya kalli Mukhtar yace "kai be babba. Me ya faru?" Mukhtar ya dago kai yana kallona,. Na dauke kai na kalli gefe sai naji ya fara magana "kun san dama ba so na take yi ba, Dole ce ta saka ta aure na, To tunda akayi auren da ma bata……..bata…..…..batayarda…………da……..daniba, Na fahimci hankalin ta yana kan wani tsohon saurayin ta da take so. To sai jiya…. nayi kokarin gain mun daidaita auren mu mun samu fahimtar juna ita kuma taki yarda, sai nayi kokarin gain na fahimtar da ita, ashe ta ajiye allurar bacci a tare da ita, shine tayi min allura" ya fada tare da fito da syringe din da nayi masa allura da shi ya ajiye a gaban Daddy. Ya cigaba "daga nan ban san me ya faru ba sai farka wa nayi na ganni ni kadai a dakin cikin halin da Yaya ya tarar da ni. Ban san ma tayi min rubutu a fuska ba ban kuma san dalilin da yasa tayi haka ba". Umma tace "to kunji dai Dama ai an gaya mana tana shaye shaye, shine ta tafi da kwaya tayi masa allurar ta. In ba yi take yi ba a ina ta samu? A ina za ta samu?" Mommy tace "munji bangare daya saura daya bangaren. Kiyi shiru dai tukuna kar kizo kiji kunya. Wannan shawara ce na baki kyauta" Umma tace "Mukhtar dai wannan wallahi na san tarbiyyar da na bashi kuma ko a gaban wa zanyi shaidar sa..... ." Mommy tace "ni ma na san tarbiyyar da na bawa Safiyya amma ba zanyi shaidar ta a gaban mutane ba sai dai in barta tayi proving tarbiyyar tata da kanta. Ba'a shaidar yayan zamani, Wannan ma wata shawarar ce na baki kyauta". Cikin fada Uncle Ahmad yace "kunji kunya dai kam wallahi. A gaban yayan ku kuna fada kamar kaj'" sai ya juyo ya kalle ni '"muna jin kike kuma. Ga abinda mijin ki yace. Me zaki ce akan hakan?" Kafin inyi magana Mukhtar ya cigaba "Abba ni dai ina son matata. Duk abinda ya faru kuskure ne da rashin fahimta a tsakanin mu. Ina rokon a bamu dama mu tattauna a tsakanin mu mu daidai ta. Ni dai ina son matata kuma na yafe mata abinda tayi" Umma ta rafka salati "la ha ila ...... ... Kaji shanyayye" Mommy tayi dariya "kunya ta farko ta tabbata" Daddy yayi magana "ba zaku yi shiru din ba kenan? In ba ku ji maganar mu ba ta yaya kuke tunanin su zasu ji maganar mu?" Uncle Ahmad ya sake ce min "muna jin ki Safiyya, kinji abinda mijinki yace, ko zaki iya kare kan ki?" Na mike tsaye na dawo tsakiyar su sannan na juya ina kallon Mukhtar nace "na gaya maka tun a jiya. It is going to be your words against yours not mine" sai na dauko wayata daga jakata and I played the audio of maganganun da muka yi da shi that I recorded, maganar ta fara ne tun sanda ya farko "safffiyya. Me kika yi min . And it ended with "no, it is going to be your words against yours" Duk da akwai maganganun kunya a ciki amma banji kunyar su ba haka na bari suka ji komai. Suna gama ji na dauki wayata na koma inda nake zauna na zauna. Mommy ta kama salati "la haula wala..Yau naga abinda yafi karfina ni Sa'adatu" Uncle Ahmad ya mike tsaye "Mukhtar! Ka gaya min cewa ba kai bane ba kake magana a cikin wayar can, gaya min cewa ba kai bane ba" Umma tace "'uhm uhm. Ku barshi yayi magana dan Allah, na tabbatar yana da bayanin da zaiyi mana. Na tabbatar akwai explanation to all these" Mommy tace "wanne bayani bayan wanda muka ji? Ko kuma ba muryarsa bace wannan? Ji nake yanzu ya gama cewa shi da ya farka ma bai ganta a gidan ba already ta tafi. Ko cikin bacci suka yi wannan maganganun?" Mukhtar gabaki daya ya rikice, ac ce a falon amma gumi yake hadawa kamar anyi masa wanka "Abba wallahi. ...... Daddy ka tsaya kaji ... Umma na rantse ....." ''Wallahi me? Fadi abinda zaka ce mana" yace "Abba she drugged me, Yarinyar nan ta wuce duk inda kuke tunani. Trap ta hada min. She threatened me. Scissors fa ta dauko tace zata yi min illa, kuna jin ta fa a cikin maganganun. I told her what she want to hear dan kar ta illata ni. Amma karya take yi min Abba. Ni ban san komai akan abinda ya faru da ita ba. Dan Allah Abba ka yarda da ni". Na rufe ido na ina jin zuciya ta tana tafasa, na bude na kalli Daddy naga yana zaune ya dafe kansa sai maimaita salati yake yi shi ya kasa ma magana. Na sake kallon Mukhtar naga yadda ya dage yana ta jera wa iyayensa karya da fatan lallai sai sun yarda da shi. Sai naji Abba yace "biri dai kam yayi kama da mutum. Idan har abinda ya faru da ita kenan da tuntuni me yasa ba ta fada ba tun a lokacin sai yanzu tukunna? Me yasa ba ta ce tana zargin sa ba sai ta amince ta aure shi dan ta makala masa wannan sharrin? Me yasa da farko da yace yana son ta ta ki shi sai daga baya kuma da kanta tace tana son auren sa, ya kamata mu duba wannan maganar, Yaya ya kamata muyi dogon bincike kafin mu yanke hukunci", Mommy tace "amma me yasa yayi karya? In yana da gaskiya me yasa yace bai ma san sanda ta bar gidan ba bayan gashi munji sai da suka yi maganganu kafin ta fita?" Suka cigaba da maganganun su yayin da ni kuma na kwantar da kaina kawai akan kujera ina jin su, na fahimci iyayen Mukhtar gabaki daya kokari suke yi sai sun kare dan su sun ce sharri nayi masa, ni kuma nawa ban ya kasa cewa ma komai saboda rashin lafiya sai fuskar sa da take nuna tsananin damuwa, sai Mommy ce kawai bakin ta yaki yin shiru sai kokarin mayar wa da su uncle Ahmad maganganun su take yi. Na bude ido na ina kallon su, a raina nace plan C it is. Sai na jawo jakata ba tare da sun lura ba na dauki scissor dina na boye a cikin hijab dina na mike tsaye na fara magana. "okay shikenan. Yanzu kunce sharri nayi masa. Gashi kunji da bakinsa ya fada amma Umma tace "me muka ji ya fada? Dauko wayar ki sake kunnawa. Ni dai banji inda ya amsa yayi wanna mummunan abun ba" nace "ba zaku yarda ba dama. Ni na san ba zaku yarda ba. Wai kuma a haka Daddy yana da rai kenan. Idan babu shi kuma fa? Me zai faru idan babu shi?" Uncle Ahmad ya mike a zuciye "ke Safiyya ki shiga hankalin ki, kar ki gaya mana maganar banza. An gaya miki kudi hauka ne da zaki saka mu a gaba kina daga mana murya da maganar banza alhalin mu iyayen kine?", Na girgiza kaina ina jin hawaye yana bin fuskata "maganar banza. Maganar banza kake cewa uncle" na juya ina kallon Mukhtar da dacin rai nace "you took everything from me. Duk abinda na mallaka, duk abinda nake takama da shi sai da ka raba ni da shi, mutunci na a matsayi na na ya mace, daraja ta a cikin al'umma, soyayya da amincin iyayena, my confidence, my good image, saurayina xa nake so fiye da komai sai da ka raba ni da shi saboda abinda kayi min, you almost took my sanity dan sai da na kusa zaucewa saboda bakin cikin abinda kavi min and I promised you tun a lokacin kuma yanzu ma a gaban iyayen mu ina maimaita maka, i will take away everything from you too ko da kuwa duk abinda na mallaka zai kare akan hakan. Bayan na gama nawa kuma I will make sure you get the highest sentence da za'a ¡ya yiwa rapist a Nigeria". Gaba daya duk sunyi shiru suna kallo na, ni kaina ban san cewa da karfi nake maganar ba sai da nayi shiru. Hawaye ne kawai yake bin fuskata ina zagaye su, Sai na saka hannu na share hawayen fuskata a dai dai lokacin da na tsaya a saman kan Mukhtar da yake zaune a kasa a gaban mu. Ba tare da sun lura da abinda yake faruwa ba kawai sai na durkusa na damki gashin kan Mukhtar na yanka da almakashin hannuna, making sure na dan yanke shi kadan. Ya zabura saboda zafi ni kuma na mike da gashin sa a hannuna. Na nuna masa almakashin hannuna nace "I told you zanyi amfani da shi dama. Ga abinda zan yanka nan" na koma inda na ajiye jakata na bude na dauko ledar da na ajiye a ciki ta ziplock na saka gashin a ciki sannan na ajiye ta a tsakanin uncle Ahmad da Daddy nace "zan kawo muku na yaron da na haifa. Run a DNA test ku gani idan ba nashi bane ba. Idan kunyi baku yarda ba ku sake asibiti ku sake yi and I assure you ko sau dari zakuyi zaku ga 100% compatibility. Dan sa ne". Mukhtar ya mike yana kallona, daga dukkan alama maganar da da nayi ta mantar da shi zafin yankar sa da nayi, yace cikin kidimewa "you told me he is dead" na daga kafada "I lied" na koma na zauna, Daddy yayi magana murya can kasa "wanne irin dead kuma? Yaushe? Jiya mana ganshi on a video call". Mukhtar ya zame saura kadan ya fadi sai ya zauna akan kujera tare da dafe kansa, cikin karyewar zuciya ya sake cewa "you told me he is dead" na sake maimaita wa nima "I lied", Daddy ya saka hannu ya dauki gashin Mukhtar da na ajiye a gaban su, sannan ya dago kai yana kallon Mukhtar din fuskar sa cike da emotions da ba zan iya kwatantawa ba yace "idan har ta tabbata kaine Mukhtar. Idan har ta tabbata kaine, wallahi, wallahi, sai na tabbatar da cewa kayi nadamar zuwa duniya". Ya zame daga kan kujerar da yake kai ya sauko kasa, in ka ganshi zaka dauka sanarwar cewa Umma ta mutu aka kawo masa. Ya bude baki ya kai sau biyar amma ya kasa furta komai. A karshe sai yace "Daddy..... Abba ..... Dan Allah.…” Na mike ina kallon sa nace "I will see you in court" har zan fita kuma sai na juyo na nuna uncle Ahmad nace "kai kuma ka dawo min da kudin da ka sata nan da one week ko kuma ka kawo min resignationletter din ka". Na juya na fita, Yes, I know that last part was petty and uncalled for but I didn't care. I was beyond caring. Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Four : Betrayed Not edited…. Dakina na koma da sauri kamar wadda ake hankada, ni raina a matukar bace. Yes na san dama iyaye suna son yayansu and it is only natural for iyaye to choose yayan su over every one else, but that should be on something not as serious as this. Sanda abin ya faru da ni musamman sanda maganar cikina ta bayyana every hand was pointing toward me akan abinda ni nasan bani da laifi akai amma babu wanda ya yarda da ni, to me yasa yanzu ba zasu juya hannun su nuna wanda yake da laifin ba sai suke neman shield din da zasu kare shi da shi? Me yasa ni lokaci daya aka yarda nayi laifin amma shi ba za'a yarda yayi ba? But they are all in for a surprise. Zasu sha mamaki na ba kadan ba. Dan tabbas Mukhtar sai ya girbi abinda ya shuka sai dai in lahira zasu kai shi su boye shi. In can din ma suka kaishi walakiri yana can yana jiran shi, dan ban yafe masa ba kuma ba zan taba yafe masa ba. Na shiga dakin na koma na zauna akan kujerar da na tashi daga kanta ina mayar da numfashi. Babu wanda zai fahimci abinda nake ji a zuciya ta sai wanda ya taba shiga cikin irin halin da nake ciki. Babu kuwa wanda nake yiwa fatan ya shiga irin halin da na shiga a rayuwata. Na sha wahala. Na wahala ba kadan ba. The pain and trauma of the rape was the easiest part, sharrin shaye shaye da Mustapha yayi min, kin yarda da ni da Daddy yayi da kuma yadda maganar ta fara kokarin juye wa zuwa kan Muhammad duk ba sune worst abinda ya fi bakanta min ba. My life got totally destroyed lokacin da na fahimci ina da ciki. . . . . . 11 months ago Immediately after the night to remember….. Ba makaranta ba, a Abuja ma Daddy bai barni ba ya dauke ni muka koma Kano tare, a lokacin babban tashin hankali na shine Muhammad, na san yana can cikin damuwa akan bacewar da nayi na barshi a ranar da na saka masa rai na kuma yi masa alkawarin zan kaishi wajen mahaifina. I tried calling him amma sai na kasa saboda babu abinda na wuni a ranar ina yi sai kuka, muryata har dashewa tayi, kuma yadda muke da fahimtar juna ni da shi na tabbatar yana jin murya ta zai san wani abu ya faru da ni, ni ma kuma na san ina jin muryarsa zan sake wani kukan dan it will remind me of all the love and the promises da muka yi wa junan mu. Dan haka sai na tura masa text, na gaya masa cewa bayan ya fita aka kira ni cewa Daddy sun zo amma jikin sa ya tashi, shi yasa na tafi na barshi dan hankali na ya tashi. And I forgot my phone in the car shi yasa ban dauki kiran sa ba. Nace masa kuma da muka kwana a asilitin jikin baiyi dadi ba sai muka sake fita dashi da ga kasar, shi yasa ba zai same ni a waya ba ko ya kira. Daga nan na rufe dukkan sims dina yadda ko ya kira ba zai samu ba. But I cried after that, just the thought of him yana kara sakani bakin ciki da bacin rai. Tun a lokacin naji na fara tunanin rabuwa da shi. A ganina bai yi deserving a used rug like me ba, Tun kafin muje kano Mommy ta samu labarin wai na zo gida a buge kuma bincike ya nuna cewa saurayi ne yaje makarantar mu ya dauke ni ya fita da ni. Na kuma san wanda ya bata labarin.... Abinda ta fara saka ni a gaba da tambaya muna zuwa gida shine waye saurayin nawa? "'Wanda kika ce zai zo gurin Daddyn ku ne? Dama ba mutumin kirki ba ne ba Safiyya? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, abinda kika zama kenan Safiyya?" And then….. "Na gaya maka dama baban Mustapha, yarinyar nan aure za'a yi mata kaki yarda. Tun da ta nuna auren ta ke so to ai auren ya kamata ayi mata. Ga Mustapha nan yace yana son ta amma daga kai har ita kun nuna ba kwa son abin. Gashi nan ai ta fara kula wadanda ba mutanen kirki ba. Bayan ga wannan wanda kai kayi tarbiyyar sa da kan ka". Naji kamar zuciyata zata kama da wuta, Wata irin tsanar Mustapha tana kara shiga ta. A zuciya ta ina kara tabbatar wa da kaina cewa shi ya aikata min wannan aika aikan dan ya cimma burinsa, dama ya jima yana nema ya ga tabbas ba zai sa mu ba, ya shigo da maganar aure ba dam yana so na da gaske ba sai dan kudin da yaji an ambata a matsayin nawa, shima kuma ya ga babu nasara ta wannan bangaren shi yasa yayi min wannan abun, sannan kuma ya kala min sharrin shaye shaye, dan a matsamin dole in aure shi shikenan ya samu riba biyu. Ni kuma tun a lokacin nayi rantsuwa a raina cewa ko mazan duniya zasu kare ba zan aure shi ba. Na kuma rantsuwa cewa sai na tona mass asiri. Amma kafin in tona masa asirin ai dole sai na bayar da labarin abinda ya faru da ni sannan in shigar da maganar wanda nake zargi. Amma kuma maganar tayi min nauyi da yawa a bakina, a zuciya ta. A cikin first few weeks da faruwar abin na gwada bude bakina in fada yafi sau a kirga amma sai dai in mayar da bakin in rufe ba tare da na fada din ba saboda maganar taki fitowa, Magan6ce da bazan iya yin ta da Daddy ba duk kuwa da shakuwar da take tsakanin mu, ita kuma Mommy da ya kamata inyi maganar da ita dan ta nake zargi da aikata min wannan abun dan haka ita ma sai ma kasa bude bakina in gaya mata, Sai dai kuma tun da abin ya faru sai na rasa lafiya. Farko tsananin ciwon jikin da ma dangantashi da abinda ya faru, sai kuma ciwon kan da nayi tunanin tashin hankali ne da bakin ciki ya saka min shi, daga nan bayan sati biyu sai abin ya wuce ya zama zazzabi. Mommy ta kaini asibiti suka yi min gwaje gwaje suka bani magunguna har da su karin ruwa, kwana na biyu aka sallame ni na dawo gida na fara pretending kamar na warke saboda yadda nake tsoron allura, amma kuma sam ban warke ba din, tun ina boye ciwon har na kasa na cigaba da bayyana shi aka sake mayar da ni asibiti, suke typhoid suce malaria haka dai muka yi ta fama. Haka na cigaba da zama a gida ina jinya ta ina kallon Safina tana zuwa makarantar ta ni kuwa an rabo ni da tawa makarantar kuma babu ma zancen komawa ta ko kuma sake min wata. Daga cikin tashin hankalin da nake ciki a lokacin shine maganar Muhammad, ga mamaki na ya yadda da karyar da nayi masa, da na samu mukayi online call ma he sounded so genuinely concerned about jikin Daddy har yana tambayar in akwai abinda zai iya yi to help. Sai kawai na saka masa kuka, ina tausayin sa ina kuma tausayin kaina. Ina kuma jin haushin kaina akan karyar da nake ta shirga masa, amma abinda ya faru da ni abu ne da budurwa ba zata iya bude baki ta gaya wa saurayin ta ba. Through all these emotional rollercoaster da nake ciki I missed my period ba tare da na fahimta ba sai one week after lokacin da ya kamata in ga period din, ranar da nayi realizing na shiga toilet ne da niyyar yin wanka na shire kayana kenan and I noticed change a kirjina, farko ban yi wani giving much thoughts to it ba sai daga baya bayan na fito daga wanda ina shafa mai sannan na sake fahimtar chanjin and my first thought was abinda akayi min ne ya saka naga wanna changing amma ban kawo ciki ne ba, sai bayan nazo saka kaya sannan na ga pad a cikin drawer and it occured to me that ya kamata a ce nayi period. Na dauko waya ta da sauri na duba app din da make tracking period dina da shi and it shows 8 days late. Sai da ma yanke jiki na fadi. Allah ne kasai ya saka banji ciwo ba amma na jima ban dawo cikin hayyacina ba amma tashin hankalin da na shiga ciki ba xai misaltu ba. "Allah, Allah, Allah" kawai nake maimaita wa, na ma rasa me zan roki Allahn, na rasa me zan ce masa. Kukan ma a ranar bai zo ba. Hijab dina kawai na saka na dauki jaka ta tare da key din mota na fita da sauri, Safina da take falo tana kallon series hankalin ta a kwance tayi ta min magana amma ni ba ma jinta nake yi ba na fice da sauri. Abinda nake lissafi kawai shine inda zan je in tabbatar da zargin da nake yi sannan kuma in ya tabbata in fitar da shi. A lissafi na sati biyar kenan dan haka bai kai matsayin da zai zama laifi in na zubar da shi ba, sannan kuma na taba jin waazin da aka ce idan rape case ne irin nawa malamai sun yi saasauci akan hukuncin zubar da shi. Sai dai o bayan da na fita daga gidan da mota ban san inda zan dosa ba. Ni dai na san ba zanje gurin likitan gidan mu da wannan zancen ba dan idan yaji to kamar Daddy yaji ya gama ne, ni kuma zan iya bayar da raina a lokacin dan kar Daddy yaji wannan maganar. Haka nayi ta yawo da mota a titinan garin kano ban san inda zan je ba. Cikin ikon Allah kawai sai naga signboard din wani asibiti a bakin titi, I followed the directions sai gani a kofar asibitin, dan karamin clinic ne haka, Na shiga na je reception din su na nemi gain likita suka ce sai na bude file na bada kudi suka bude min na cike info din da duka nema amma ko kadan ban saka addres dina na gaskiya ko number wayar wani a gidan mu ba. Daga nan naje na hau layi, babu abinda nake yi sai salati da istigfari a zuciyata ina rokon Allah yasa kar zargi na ya tabbata, a haka layi yazo kaina na shiga gurin likitan direct na gaya masa pt nake so ayi min. Ya tambaye ni symptoms dina na fada masa sai ya rubuta min test din yace inje lab suyi min, na je lab din suka dauki jini na, for the first time in my life aka huda jiki na ban ma san an huda ba dan zafin da nake ji a raina ya ci uban zafin allurar. Ina zaune dai har aka gama, zuwa lokacin na tabbatar an fara nema na a gida dan dai har lokacin layi na a kashe yake da an fara kira na. Hankali na idan yayi dubu ya tashi. A haka aka rubuta min result din aka ce in mayar wa da Dr. Ban mayar din ba na samu guri na zauna na bude takardar da sauri ina bin rubutun da kallon ina neman kalmar positive, and I saw it, and it was the worst news I have ever received in my life, Tashin hankalin da ma shiga baya misaltuwa, dan yafi ma na ranar da aka yi raping dina, kawai hango kai na nake yi a gaban Daddy da ciki a jiki na, musamman a yanzu da na san in dai ba miracle ba ba lallai ya yarda rape ba ne ba, and then sai na hango Muhammad, na hango Muhammad idan labari ya iske shi cewa Piya ta yi cikin shege. Naji na tsani kaina, na tsani rayuwata, na tsani duk wan abu da ya shafe ni and most importantly na tsani cikin jiki na. Zuwa lokacin magrib tayi na tabbatar cewa in na koma gida ina cikin matsala but still ban koma din ba. Dan matsalar da nake ciki ta fi ta kaiwa dare a waje Na rufe takardar na juya na koma office din Dr na kai ma sa sannan na zauna ina kallon sa har ya gama karantawa, ya dago kai yana yi min murmushi "well, congratulations madam. You will soon become a mother" na gyara zamana ina kallon sa directly nace "ina so zan zubar da shi, kuma yi?" Ina kallon yadda murmushin ya bar fuskarsa sannan ya fara yi min wani irin kallo mai cike da zargi, a karshe yace "mu mutanen kirki ne a asibitin nan, ba ma yin irin wannan aikin asshan….." Ban jira sauran maganar ta sa ba na mike na dauki jaka ta na fita.Sai da na koma mota sannan na kife kaina na kama kuka, nayi kuka kamar raina zai fita. Me zance da Daddy in ya ganni da wannan cikin? Me zance da Muhammad, I couldn't imagine yadda wanna maganar zata yi breaking heart dinsa. He doesn't deserve this. Na tuna da sauran yan'uwa na da kawayena wanne irin tunani zasu yi a akaina, probably most of them zasu yi min irin kallon da wancan dr din yayi min ne. Yar iska, tayi yawon banza tayi cikin shege Na kuna mota ta amma maimakon in koma gidan still sai na cigaba da yawo ina neman wani asibitin. Ni tunda na tashi ban taba zuwa asibiti da kaina ba, muna da likitan da yake zuwa ya duba mu in bamu da lafiya, in ciwon yayi karfi kuma a kaimu asibitin sa, duk ban san was formalities na harkar asibiti ba. Bayan tsahon lokaci na kuma gain wani asibitin na sake shiga, sai suka ce min Dr din ba ranar yake zuwa gain patience ba sai dai nurse, na je gurin nurse din and I told her directly ga abinda nake son yi, a take ta fara yi min wa'azi har da janyo aya da hadisi, ban barta ta sauke wadda ta janyo ba na dauki jakata na fita na bata guri. Zuwa lokacin na san dole ne in koma gida ko dan gudun kara wa kaina laifi akan wanda already nake da shi. Da kuma lafiyar Daddy. Haka na ja mota nayi gida, idanuwa na har sun kumbura saboda kuka. Ina zuwa kofar gate kuwa naga karamin munafikin, Mustapha, kafin mai gadi ya bude min kofa ya zo window na "daga ina kike?" Ko kallon sa bani ba na ja mota a guje na shiga, ina shiga kuwa na hango Daddy a tsaye a kofar shiga side dinsa, ina yin packing ya taho gurin motata, a dai dai lokacin da Mustapha shima ya karaso, Daddy ya tambaye ni "daga ina kike?" Na fara kokarin furta karyar da na shirya zan fada idan an tambaye ni "gidan su kawata na je na karbo sako" ya na kallon fuskata yace "karbo sakon ne ya saka ki wannan kukan?" Na yi sauri na shafa fuskata, a hannu ma naji alamun ta kumbura. Mustapha ya warce jakar hannuna "Daddy gwara a duba a ga wanne irin sako ne ta karbo" ya fada yana kokarin bude jakar, Daddy ya dakatar da shi "kar ka bude mata jaka" amma kuma sai shi ya karba "bani inga" na gode Allah da ban karbo takardar lab result dina ba, Daddy ya bude jakar ya duba kayan ciki sannan ya miko min yace "je kivi sallah ki zo ki same ni a daki" ya juya ya koma ciki. Na juya nima zan shiga ciki Mustapha ya biyo ni a baya "Allah ya taimake ki. Amma wata rana za'a kama ki ne" na juyo a fusace "za'a kama ni ko za'a kama ka? Ka jira karshen ka Mustapha. Wallahi karshen ka ba zata yi kyau ba". A ranar Daddy har cikin bedroom dinsa yayi kira na muka zauna "Safiyya, me yake damun ki? Ki gaya min in kina da wata damuwa. Wani abun aka vi miki? Wani ne a gidan nan yake takura miki?" Amma in na bude baki sai in mayar in rufe, duk yadda naso in gaya masa sai na kasa gaya masa and I missed Ammie sosai da sosai. A karshe dan ya bar tambaya sai na ce masa "bana son zancen aure na da ake yi da Mustapha. Bana son sa" Daddy yayi ajjiyar zuciya "shikenan damuwar? Ke waye yace miki za'a aura miki Mustapha? Dan kinji mahaifiyarsa tana maganar ai hakan ba yana nufin maganar ta tabbata bane ba har zaki zauna kina irin wannan kukan. Ni bani da niyyar yi miki aure yanzu. Idan kuma lokacin auren naki yayi bani da niyyar yi miki auren dole, ke zaki zabi wanda kike son aura ki kawo min shi, idan na ga ya cancanta sai in bashi ke, kinji? Ki daina da mun kanki" na gyada kai kawai na tashi zan tafi, har na kai kofa sai yace "kuma karki sake fita ba tare da kin gaya wa Sa'adatu ba". Amma damuwa fa a lokacin ne ma na fara yin ta. Yadda nake gain rana haka nake ganin dare, burina kawai shine in samu yadda zanyi in raba kaina da cikin da yake jiki na dan with each passing day na san lokaci ne yake cigaba da kure min. Kuma sai a lokacin sannan laulayi ya kara saka ni a gaba. Wannan ya sa a daki nake wuni ni kadai kuma haka zan wuni ina zaryar amai a toilet. Ranar nan dai na je nayi wa Mommy karya "Mommy akwai kawata Sharifa, kin tuna ta? Mun jima ba mu hadu na kuma na rasa number dinta, ina so zanje gidan su mu gaisa" sao naga taji dadin haka "yauwa ko ke fa? Ai gwara ki fita ki dan ga gari kiji dadi amma ace kullum mutum yana kwance a daki" har na fara murna sai cewa tayi "sai ku tafi tare da Safina". A haka plan dina ya rushe. Ina ji ina gani haka naje nayi zumuncin da banyi niyya ba. Muka wuni muka dawo gida babu yadda zanyi. Ranar nan ma na sake satar kafa naje wani asibiti da nake gani a hanya muna wuce wa shima nay demanding abortion, suma suka ce min basa yi tare da hada wa da yi min wa'azi, sai na fito na tafi wani Asibitin da naga kamar ba musulmai ne suke running dinsa ba dan kar suyi min wa'azi amma suma sai suka ce is against there their religion and medical ethics, har da gaya min wai Jesus yana sona yana kuma son abinda yake ciki na. Haka na fito suma ban samu abinda nake so ba. A lokacin da cikin ya kai wata biyu ne na yanke shawarar neman sunan abortion pill din online sai inje in siya. Nayi searching ma samu sunan wani da naga a review dinsa kamar yana da kyau, haka nayi ta yawo shima na rasa chemist din da zasu siyar min sai suke wai sai da saka hannun likita. Daga baya na fahimci cewa duk inda nake zuwa gurare ne na mutane masu mutunci, abinda kuma nake bukata ba abu ne da ya shafi mutunci ba. Ni kuma ko kawaye da zan iya yiwa irin wannan tambayar bani da su. Dan haka na dauki mota na tafi kasuwar sabon gari, haka nayi ta yawo a kasuwar nan da kyar na samu chemist na shiga na basu kudi da yawa suka bani wani magani suka ce inje gida in sha. Amma hatta shi mai chemist din sai da yayi warning dina cewa akwai ciwo kuma zan zubar da jini but I didn't care, Ina zuwa gida na shige dakina na rufe kofa sannan na debi maganin na watsa a bakina na bisu da zuwa. A ranar ban dauka cewa zan sake kwana a duniya ba, Ban taba jin ciwo irin wannan ciwon ba, Ji nayi kamar allura aka samu ake caccaka min a mara ta. A take kuma jini ya tsinke min, jinin da na zubar na dauka jinin jikina gabaki daya ya kare kenan, dan ban ma dauka akwai adadin wanna jinin a jikin nawa ba. Ban sani ba azabar ciwo ne ko kuma yawan jinin da na zubar ne ya dauke ni ba, ni dai na san na fadi a cikin toilet. Sanda na farka akan gado na na ganni a kwance, a gefe na kuma Mommy da Safina, Mommy ta ci kuka idonta yayi ja, hannun ta rike da packet din maganin da na sha. Na mayar da idona na rufe ina in duniya gabaki daya tayi min kunci, yanzu shikenan Mommy ta sani, shikenan Daddy zai sani, shikenan na shiga uku, me yasa ban mutu ba. Mommy ta fara magana "yanzu sakayyar da zaki yi mana kenan Safiyya? Reward din mu kenan na duk tarbiyya da kulawar da muka baki? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" na kasa bude ido na sai hawaye kawai da ya ke bin fuskata. Naji Mommy tace da Safina "je ki ce masa ta farka" nayi sauri na bude ido ina kallon kofar shigowa kirjina yana dukan tara tara, daga dukkan alama dama yana kusa da dakin nawa dan bata dade da fita ba ya shigo, fuskarsa kawai na kalla na fashe da kuka, hannayensa nannade da belt din da ban san ma a ina ya samo shi ba, amma sam ban ji ina jin tsoron ya dake ni ba, ni damuwata shine din da na gani a fuskarsa. Na zamo daga kan gadon na zube a kan kafafuwansa ina kuka, maimakon dukan da ya shigo da niyyar zai yi min shima sai ya durkusa a kusa da ni mukayi ta kukan tare, kukan sa ya fi komai tayar min da hankali, ban taba ganin sa yana kuka ba. Mommy ma ta zauna a kusa da shi ita ma tana yin nata. Sai da ya gama kukan sannan kuma ya tashi ya fita da sauri, jimawa kadan sai gashi nan ya dawo hannunsa rike da wata katuwar wukar da ban san inda ya samo ta ba. "Kashe ki zanyi yau. Yau sai na raba kanki ga gangar jikin ki. Ni zaki nuna wa iyaka ta a duniya? Ni zaki tozarta ki ciwa mutunci Safiyya? Lahira zan tura ki kije can kiyi bayani. Wallahi ko ki gaya min wanda yayi miki wannan aika aikan ko kuma yau a lahira zaki kwana dan uban ki" Ko motsawa banyi ba daga inda nake dan ni da zai tura ni lahirar ma da sai nafi jin dadi. Mommy ta tashi da sauri ita da Safina, Mommy ta rike hannunsa tana salati "mun shiga uku, menene haka? Kayi hakuri zata fada, zata fada mana ai, Kawo wukar kar kaji wa kan ka ciwo da ita" ni dai ko kallon su bana yi har su ka gama abinsu ina dunkule a guri daya. Sai na sake jin muryar Daddy a saman kai na "Safiyya! Waye yayi miki ciki? Waye yayi miki ciki na ce?" Ya fada cikin tsawa duk da rashin lafiya ta saka muryarsa bata fitowa sosai. Na daga kaina na kalle shi da idanuwa na wanda da kyar nake iya bude su. "Daddy..... Wallahi........ Ban sani ba" na fada cikin karyayyiyar murya, ni kaina da na fadi maganar na san ba yarda zai yi da ita ba kuma wanna shine abinda yafi komai damuna. "Baki sani ba?" Suka tambaya a tare shida Mommy '"baki sani ba fa kika ce" na mayar da ido na na rufe ina fatan Allah ya dauki raina. "Zaki yi magana ne ma, zaki bude idon nan kiyi magana ne" ya fada cikin haki, kafin in ankara naji saukar belt din da ya shigo da shi dazu a hannunsa a bayana, azabar dukan har cikin kwakwalwa ta saboda ni ba dukana ake yi ba, ko a makaranta ba duka na aka taba yi ba, Na kwanta a gurin tare da dunkule wa a guri daya, ban san adadin bulalar da yayi min ba, ban kuma sani ko zafin dukan ne ko kuma tsananin tashin hankalin da nake ciki ba, ni dai na san na fita daga hayyacina, Sanda na sake farkawa a asibiti na ganni, ina kwance da karin jini a hannuna. Gefe naga Mommy nan a zaune ta rafka tagumi tana kallo na. Na bude ido ina neman Daddy amma ban ganshi ba. Tace "yana gida. Na san shi kike nema. Yana gida ba shi da lafiya. Kin sani sarai ai bashi da lafiyar amma kika he kika jawo mana wannan abin kunyar Safiyya. Wai ke yanzu har kin san kiyi cikin shege ki kuma sayi abortion pill ki zubar da shi. An tambaye ki uban sa kuma kince ba ki sani ba. To a ruwa kika sha? Ko kuma saboda yawansu ne ya saka baki san mana waye a cikin su ba?......" Na jawo hannayena biyu na toshe kunnuwana da su sannan na rufe ido na. Kwana na biyu a asibitin aka sallame ni. Bleeding din ya tsaya kuma anyi min karin jini sannan an bani magunguna, sai dai har muka tafi ban sani ba ko asibitin sun san abinda ya faru da ni ko kuma wata maganar daban Mommy ta fada musu. Har aka sallame ni Daddy bai zo ba. Ranar da aka sallame ni din ba gida muka tafi ba sai naga Mommy ta kai ni wani asibitin da ban, Muka shiga office din dr din muka zauna sai tace "yarinya ce tayi abortion, so nake a duba ta a gani in ya fita gabaki daya ko kuma in akwai saura" wannan shi ya kara tabbatar min wancan asibitin basu san abinda ya faru ba. Likitan mace ce, ta saka na kwanta akan gadon da yake kusa da ita tayi scanning mara ta sannan tace da Mommy "ya fita gabaki daya. Amma yanzu zan bata wasu magunguna da zata ringa sha wadanda zasu kara wanke mahaifar ta sosai su kuma taimaka mata gurin healing" na ji dadi ya kama ni kamar an saka ni a aljanna. Na sauko daga gadon na zauna sai ta debo magunguna masu yawa ta bawa Mommy ta kuma yi mata bayanin duk yadda za'a sha su. Ta juyo tana kallona tace "akwai possibilityn cewa period din ku ba zata dawo da wuri ba, har sai komai ya daidaita a mahaifar ki sannan period zata dawo" na gyada kai da sauri cikin amincewa, who period help? In dai cikin ya fita ai shikenan. Muna zuwa gida Mommy ta kaini wajen Daddy yana kwance a dakin sa, tsananin damuwa a tare da shi. Na zauna a gabansa na fara kuka. "Daddy am sorry" ya mike zaune yana kallo na da irin kallon da ban saba ganin yana yi min irinsa ba yace "Safiyya, cikin waye kika zubar?" Na fara goge hawayena dan nasan amsar da zan bashi ba zata gamsar da shi ba amma haka na fade ta "Daddy wallahi ban sani ba" ya koma ya jingina da jikin kujera yana cigaba da kallo na "kina gaya min cewa haka kawai kika ga ciki a jikin ki ba ki san yadda aka yi ya zo jikin naki ba?" Nayi shiru bance komai ba sai yayi min tsawa "answer me!" Na bude baki cikin rawar murya nace "na sanj" yace "to waye?" Nace "Daddy ban san waye ba. Daddy dan girman Allah ka yarda da ni. Wallahi ban san waye ba. Amma ni Mustapha nake zargi" ya bude ido cikin mamaki "Mustapha? Wanne Mustaphan?" Nace "yaya Mustapha na gidan nan" ya gyara zama "kina da hujja? Me yasa kike zargin sa?" Sai na bashi labarin abinda ya faru ranar da ya dawo daga Cyprus, tun daga farko har karshen abinda na sani. Sai da na gama yace "shi waye saurayin naki da kuka fita tare?" Navi shiru ban ce komai ba ina jin daci a raina, yace "ba zaki fadi waye ba?" Na girgiza kaina "Daddy ba shi ba ne ba" yace "kuma kika ce baki san waye ba. To ya akayi kika san ba shi bane ba?" Nace "Daddy wallahi ba shi ba ne ba". Yayi shiru kamar ba zaiyi magana ba sannan a karshe yace "you just desperately want to protect him. Har kina neman ki halaka kanki, Har kina neman ki yi wa wanda bai ji ba bai gani ba sharri" nace "Daddy Mustapha fa......" Yace "shut up! You are very stupid. Kina so ki raina min hankali. Ranar da kike magana akai muna tare da Mustapha. Nine shaidar Mustapha. Lokacin da kike magana muna jirgi tare. Ko daga jirgin ya yi tsuntsuwa yazo yayi kidnapping din naki?" Na girgiza kaina "ban san yadda yai yazo ba. Ni dai na san ya kira ni a waya yace ....." "Shut up " Daddy ya sake katse ni "kar in sake jin kin ambaci sunan Mustapha a wannan maganar. Uwar sa tana iyakacin kokarin ta a kan ki. Kar ki yarda taji wannan maganar" Har zan fita sai yace "ki shirya kayan ki. Zan je India gain likita. Dake zan tafi. I am never taking my eyes off you again". Haka na shirya muka tafi India da ni da shi da Mommy da Mustapha, kullum Mommy sai ta bani magunguna na nasha religiously dan har alarm ne da ita na shan magani na, ni kuma ban yaba saka komai a raina akan maganin ba haka nake shan kayana in ta bani, ina kuma jin dadi a zuciya ta duk da na san tsakani na da Daddy yayi bacin da miracle ne kadai zai gyara amma tunanin na rabu da cikin shi yake saka min kwanciyar hankali, at least it is over, at least zan iya regaining dignity na a hankali, Watannin mu biyu a can sannan muka dawo Nigeria. Zuwa lokacin har na fara tunanin dabarar da zanyi in sake dawo da Muhammad cikin rayuwata ya zo a matsayin wan daban ba wancan saurayin da Daddy yake zargi ba, dan shi kansa Muhammad din nasan zuwa lokacin yasan karya . A lokacin ne kuma sauran buruka nana rayuwa duk suka tarwatse a gaban ido na. Ina kwance a falo kawai naji kamar motsi a ciki na. Farko na dauka iska ce, but then the movements became very distinct. It felt like wani abu ne a cikin nawa yake yin motsi. Kwana biyu na cigaba da ji, kuma motsin kamar karuwa yake yi. And then ranar nan na tsaya a gaban mirror and really looked at cikina, and I saw it. Mara ta ta daga sosai kamar ace naci abinci na koshi sosai. Ni kuma ba me tumbi bace ba. Duk koshin da zanyi cikina baya taba kai haka girma. Na ji gaba ma yayi mugun faduwa, na dora hannu na akai a hankali na taba cikin sai naji shi yayi tauri kamar wadda aka kifa wa wani circular abu a cikin. Na koma da baya na zauna akan gado cikin tashin hankali. Menene wannan din kuma? How? When? Na sauko waya ta na fara googling ciki da yadda yake and it all showed me cewa ciki na yana nan babu inda yaje. And it occured to me that wayo Mommy tayi min. Duk wahalar da nasha wata biyu da suka wuce cikin bai fita ba ashe ya hada baki da wannan Dr din suka nace mata ciki ne da ni ina son zan cire shi. Ta fara yi min fada ita ma kamar sauran doctors din tare da gaya min su basa yin haka a asibitin sai kawai na dauki jaka ta zan fita. Tace min "wait" na dakata na dawo na zauna tace min "watansa nawa?" Nace "hudu" "ina babansa?" Nace "bashi da shi" tace "yayi girma, akwai risk mai yawa. Duk wanda zaki je ya cire miki wannan cikin ba magani kadai zai baki ko allura ba, sai anyi miki aiki an cire fetus din. Akwai at least 70% chance na cewa zaki mutu" na daga kafada nace "I don't care" Ta cigaba da kallo na. "Ina iyayen ki?" Nace "babata ta mutu babana ba shi da lafiya" tayi ajjiyar zuciya tace "okay, zan yi miki, amma kamar yadda na gaya miki akwai risk sosai. Kuma ba zan yi miki a nan ba akwai private hospital dina can zaki je sai in cire miki a can. Kuma akwai tsada, zaki iya biya?" Na bude jaka ta na dauko sarkar da na dauko a cikin kayana, set ne da dan kunnen ta da abin hannu, na ajiye mata a gaban ta nace "wannan zai yi? In ba zai isa ba I can get some money too" ta dauki sarkar tana kallo "this is gold" ta fada cikin mamaki, ban amsa mata ba nace "zai isa payment din?" Ta dauka ta saka a cikin jakar ta sannan ta miko min card din ta tace "ga address nan, ki same ni a can da weekend" na karba nayi mata godiya sannan na tafi. Da weekend din na shirya, har da leka dakin Daddy da niyyar ko da ban dawo ba na mutu to nayi masa kallon karshe, sannan na kunna mota ta na tafi address din da ta bani. Ina zuwa tace a shiga dani wani daki. Ta kara maimaita min bayanin aikin da risk din sa na kuma tabbatar mata da cewa ni ban damu ko in mutu ba ko kuma inyi rai, burina shine in rabu da cikin jikina. Sai ta bani form na cike a matsayin consent form na cewa na yarda da kuma amincewa ta za'a yi komai, Sai kuma ta dauko wata takardar ta bani, a ciki naga inda zan saka phone number din wani nawa, na nuna damuwata a kan hakan, "bana son kowa ya sani" tace "'it is just protocol, saboda idan wani abun ya faru da ke, idan aikin ba'ayi nasara ba sai mu kira gidan ku su dauki gawar ki, Ko ba kwa so su yi miki sallah su binne ki?"' Nayi shiru ina tunani sannan bayi deciding ina so su binne ni. Amma kuma sai na rasa number din wa zan saka. Definitely not Daddy. Mommy kuma munafuka ce as far as I was concerned. Ni kuma bani da wani wa da zan ce a kira. Sai kawai na saka number din Mukhtar. Da kaina naje na kwanta akan gado sannan na rufe idona lokacin da naga ta dauko allura zata yi min. A raina ina lissafin ko dai in farka a duniya ko a lahira. Amma in a duniya din ne na san zan farka ne ba tare da wanna mayataccen cikin ba. Sai dai ga mamaki na sanda na farka din, ina duniyar, kuma cikin still yana tare da ni, bayan shi kuma akwai iyaye na. Naji wani rage ya kama ni, wannan likitan ta yaudare ni. Naji muryar ta tana magana "this girl is severely depressed. She is suicidal. She is going to kill herself" Mommy tace "ki daina fadar haka dan Allah" likitan tace "but it is true. Idan ba dan nayi mata wayo ba zata cigaba da neman wanda zai cire mata ne har ta samu, za kuma ta iya rasa ranta. Babu irin tsoron da ban bata ba amma bace ita bata damu ko ta mutu ko tayi rai ba. Dole ku chanja approach din ku a kanta or else you are going to lose her". Na bude ido na, wanda na fara gani a kusa da gado na shine Mukhtar. Sai Daddy da Mommy da uncle Ahmad a can gefe tare da dr din. Naji wani irin bakin ciki, shikenan Mukhtar yasan abinda ya faru dani. Wannan wanne irin abin kunya ne. Nayi sauri na mayar da ido na na rufe. Bayan an ima kadan naii uncle Ahmad yana fada "wannan yarinya ta jawo mana abin kunya da bamu taba gani ba a dangi. Yaya aure ya kamata ayi mata. Tana haihuwa ayi mata aure. Ga Mukhtar nan, dama ya jima yana son ta kai da ita ne kuka ki amincewa. Tana haihuwa sai a daura musu aure kawai" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Five: Love Na juya baya na na fara kuka feeling totally betrayed. Ina jin Mukhtar yana yi min magana amma ban ma fahimci me yake cewa ba. I felt betrayed by everyone, Mommy da ta boye kin cewa ciki na bai zube ba, Dr Salma da ta yaudare ni tace zata zubar min da cikin, Mukhtar da na saka number dinsa kuma ya kira iyaye na. Naji tamkar kowa da kowa na duniya ya tsane ni nima kuma naji na tsani kowa, Especially kaina. Uncle Ahmad ya cigaba da fada, ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba. Blaming Daddy da Mommy wai su duka bata ni bana jin maganar kowa babu wanda ya isa ya juya ni yanzu ga abinda na zama. Har sai da Daddy ya cire alkunya yayi masa magana yace ya rabu dani, musamman saboda abinda Dr tace dan haka fada ba zai yi maganin komai ba sai dai a lallaba ni. Sai uncle Ahmad yayi fushi ya fice daga dakin, Ina jin Mukhtar yana cigaba da yi min magana, making me promises na cewa babu abinda ya ragu a zuciyarsa na son da yake min kuma kamar yadda baban sa already ya fada shi ma ya yarda zai aure ni duk kuwa da abinda nayi. Ganin bani da niyyar kula shi sai ya tashi ya fita. Daga baya Dr Salma ta dawo ta zauna dani ta yi ta kokarin inyi mata magana amma na ki kulata, haushin ta nake ji ba kadan ba. Ashe wai she is a psychotherapist as well as a gynecologist dan haka Daddy ya bude min file a gurin ta wai zan ke zuwa duk sati ina ganin ta. Daga nan aka sallame ni bayan uta ma ta bani wasu magungunan. Muna komawa gida na kwanta a falo na rufe idona pretending kamar bacci nake yi sai naji Daddy da Mommy suna rigima, Daddy yana ta fada sosai muryar sa har makale wa ta ke "How can you do this! Ta yaya kin san cikin nan bai fita ba amma zaki ja bakin ki kiyi shiru? Menene hujjar ki ta yin hakan?" Tace "kana ganin da ta san da cikin da zata barshi?" Yace "nima da nasan da shi da ba zan barshi ba ballantana ita, Ke yanzu da kika barshi me zai yi miki?" Tace "I don't care about cikin, but I do care about her. Ni na san halin da na tarar da ita a ciki a wancan karon da tayi kokarin zubar da shi kuma in no way zan kuma barinta ta saka kanta a wanna halin. Likita ta gaya min cewa those pills are effective kuma Safiyya overdose din su tayi ma. Still kuma cikin bai fita ba. In dai har ta sake sha zata iya rasa ranta maimakon ta rasa cikin. In dai ta kashe kanta ta mutu kafura fa kenan, ba gwara ta haihu mu san yadda zamuyi da dan ba sannan kuma sai a guji gaba, ayi mata aure. Shi yasa na nuna mata cewa ya fita dan ta hakura har zuwa sanda cikin zai girma yadda dole ta hakura da zubar da shi. Ba a kanta aka fara ba ai. Ni dai ta bangare na nobody will know. Haka ta bangaren yaya na. Amma yanzu da su Ahmad suka shigo cikin maganar i am not so sure akan rufuwar asirin" Daddy yace "but you could have told me. Tare dani da ke ya kamata mu zauna muyi wannan shawarar. I should have had a say in what goes on with my daughter's life. Idan da kin gaya min abinda likitan tace a lokacin I would have take her to duk kasar da nasan suna da likitocin da zasu cure mata cikin successfully, Ko a Nigerian nan ma ba za'a rasa likitan da zai cire cikin few weeks ba tare da complications ba. Kuma kin san da haka. Amma kika bar marainiyar Allah da ciki a jikinta har ya kai lokacin da cire shi ya riga ya zama haramun. Wato kin bar mu da choice din ko dai mu aikata sabo wajen cire cikin ko kuma mu barta ta haifi shege and then we will have no choice then to get her married and cover up abinda ya faru, shine target din ki ko?" Mommy ta hau "how can you say that? Kana ganin zan cutar da Safiyya dan ta auri Mustapha? Abinda kake nufi kenan? I made the decision for you dan nasan duk abinda ya shafi Safiyya idonka rufe wa yake yi ba ka ganin gaskiya, duk laifin da tayi you will cover it up and find someone to blame for it. Yanxu ma kuma abinda kake yi kenan. Kana so ka juya laifi zuwa kaina ba yan kasan laifin ka ne. Ka riga ka bata yarinyar nan iyakacin bata wa. Yanzu kuma da lokacin karbar sakamako yayi you are looking for someone to blame". Daga lokacin rayuwa ta kara chanja min, duk da uzurin da Mommy ta bayar amma ban kuma jin cewa na yarda da ita ba, abinda na saka a raina shine ta vi ne saboda a matsa min lallai in auri Mustapha, Wannan kuma sai ya kara min zargin cewa Mustapha ne uban ciki na, za kuma ta iya yiyuwa cewa Mommy ta san da haka, sun hada baki ne dan su ci kudina. Daddy a bangaren sa ya rage yi min hayaniya sosai. Amma kuma ni kaina bana jin dadin zama a gabansa dan wannan bond din da yake tsakanin mu sam babu shi, bana o son kallon idonsa dan disappointment kawai nake gani a cikin su. Yayi kokarin nuna min ba komai, har sabuwar wayar da ake yayi a lokacin ya siyo min wai inyi keeping in touch with my friends tunda ba ma tare, amma ni na san yayi hakan ne kawai dan yana gudun zan sake kokarin halaka kai na. Idan nace I was depressed a lokacin sai inga kamar na rage wa abinda naji girma. Babu anar da ba zanyi wa kaina addu'ar mutuwa ba. Abu daya ne ya hanani loosing hankali na completely shine sallah da na rike na koma ga Allah. Kullum ina dakina akan sallaya, anan nake kuka na anan nake baccina anan nake wuni. Sai dai Mommy ta shiga ta loda min uban magunguna in shanye ta bani abinci in ci, Safina ma tana shigowa, amma sau da yawa in ta shiga gurina ko kallo bata ishe ni ba ballantana har muyi magana dan haushin mahaifiyarta da dan uwanta ya shafe ta ita ma. Twins suna boarding suna kokarin rubuta jarabawar kammala secondary school dan haka bani da tabbas din sun san halin da nake ciki ko basu sani ba. Ciki na kuma tun daga sanda na fahimci yana nan shikenan sai ya cigaba da girman sa kamar wanda ake hura shi kullum, tun riga tana boye shi har ya fara fitowa a cikin rigar ma sai dai in na saka babba ko kuma na saka babban hijab. A haka Daddy ya yanke wata shawara ya kira ni ya gaya min "akwai asibitin da aka yi min maganar sa a Berlin, likitocin su sun kware akan kula da masu ALS, zan je can, zan kuma tafi da ke ki zauna tare da Sufyan da matarsa har sai kin haihu. She is a good woman and a good friend of your mother's. Na san ba zata tona asirinki ba. Kafin nan kuma dole ki gaya min uban dan saboda in kai masa kayansa. And you, kina haihuwa zanyi miki aure dan ba zaki kara min wani abun kunyar ba. Besides, my time is running out and I want to see you settled before I go" Na fara kuka amma bai chanja shawarar sa ba sai ma yace in tashi in bashi guri, na shiga daki na cigaba da kuka na and I knew it was time to let Muhammad go.... Dole in hakura da shi. Tunda na san ba zan aure shi ba. Na san Daddy zaiyi kokarin aura min wanda in aka tashi auren ba za'a vi bincike ba ballantana a gano abin kunyar da nayi. Sai dai kuma na rasa yadda zan yi in rabu da shi din. Me zance masa? Dole in gaya masa wani abu da zai saka ya hakura da ni dan idan nayi ghosting dinsa just like that ba zai hakura ba zai cigaba da nema na ne har sai ya same ni, kuma ina tsoron garin neman nawa kar ya binciko abinda nayi. Kafin tafiyar mu tafi sai na yanke shawara. It wasn't the best shawara nima na sani but I wasn't on my right senses sanda na yanke ta. Ni da mahaukaciya banbancin mu kadan ne. Amma kuma a raina ina son in sake ganin sa, ko da sau daya ne. A lokacin tafiyar mu ne naci sa'a jirgin mu ta Abuja zai tashi, Daddy yaso sai ranar tafiyar mu zamu je Abuja amma sai nace "Daddy muje mu kwana mana, tunda ba ka da lafiya ka samu ka dan huta ba wai muna sauka kuma mu shiga jirgi mu tafi ba" It has been long rabonda na saka baki in ana magana, maybe shi yasa Daddy ya bi shawarata to encourage me to talk more, Ni kuma plan dina shine in samu damar zuwa ganin Muhammad, Ina ganin ya yarda na tura wa Muhammad sako cewa na shigo Nigeria, mu hadu a office din sa, akwai magana mai muhimmanci da zamu y" Muna zuwa Abuja kuwa bayan an shigar da kayan mu na shiga daki kamar zan kwanta in huta ne sai na dauki key din mota na faki ido na fice. **. *. *. *. ***. Present days….. And now, all the possible tablets have turned in all the impossible directions Mommy ta bude kofa ta shigo dakin. Ta tsaya a bakin kofa tana kallo na, sai kuma tayi ajjiyar zuciya "zaman cikin duhun dai yana nan" sai ta kunna fitilar dakin sannan ta karasa shigowa. Ta tsaya tana kallona sai kuma ta zauna a kusa dani. "Safiyya?" Ta tafa da karyayyiyar murya, sai na dora kaina a kafadar ta tare da sakin kuka. Ta juyo ta rungume ni sosai "Safiyya. Kiyi hakuri. Ya isa kukan haka nan. You have cried enough. Ya isa haka" ta fada cikin sigar lallashi. Na daga kaina ina cigaba da sheshshekar kuka. Ta kama hannuna "kiyi hakuri Safiyya. Ni ban san da wanne bakin ma zan baki hakuri ba, Daddyn ki ma haka, Kiyi hakuri dan Allah ki yafe mana rashin fahimtar ki da bamu yi ba, Wallahi yanzu dukkan mu mun yarda, ba ma bukatar ma da test din abinda muka ji da kuma yanayin Mukhtar kadai ya gamsar da mu. Mun yarda da ke. And it breaks my heart yanzu da na fahimci cewa you went through all that kuma you are innocent. Sannan kuma mu iyayen ki mun ki yarda cewa you are innocent. Kiyi hakuri dan Allah". Na gyada kai na tare da share hawaye na da hannu biyu. Sai kuma nace "ke ma kiyi hakuri, I have been disrespectful to you a lot of times" ta girgiza kai "babu komai. Ni ban taba rike ki ba. Most of the times in kinyi abu Daddyn ki nake hucewa a kan sa" sai kuma tayi murmushi "yanzu kam shima duk jikinsa yayi sanyi. Na san kunyar hada ido zaiyi da ke. In kinje gurin sa you should use kind words to ease guilt feelings din sa" nace "to Mommy sai kuma tace "su Ahmad sun tafi. Sunce zasu bincike shi sosai. But sum jikin su yayi sanyi. Uwarsa ko magana ba ta sake yi ba har suka fita. Da kyar ma ta iya mikewa da ga inda take zaune. I guess he will confess sooner or later" muka vi shiru gabakidaya sai kuma tace "kai! Allah ya isa wallahi. Raina zafi yake yi. Ji nake kamar in bisu in je gidan in zazzaga musu masifa, Wannan wanne irin zalunci ne?" Na dan yi murmushi nace "you don't need to go to them, zasu dawo ne da kafafuwan su suna begging for forgiveness and then you can talk to them in all manners da kike bukata". Sai washegari sannan a koma gurin Daddy da safe na gaishe shi kamar yadda nake gaishe shi duk safiya. Ya amsa sannan yayi shiru, nima nayi shiru kaina a kasa sai da muka jima a haka sannan na mike da niyyar bashi guri tunda naga kamar baya son muyi maganar sai kuma ya kira sunana, na dawo na zauna sai yace "me yasa?" Na dago kai da mamaki "Daddy me yasa me?" Yace "me yasa kika zabi auren Mukhtar bayan kuma kina zarginsa da wannan mugun abun? Me yasa tunda kika fara zargin sa baki zo kin same ni kin gaya min ba? Ko dan kina ganin I dismissed you sanda kika ce min kina zargin Mustapha? Haka ne? Idan da Mukhtar kika ce I would have given it more thoughts than Mustapha. Me yasa baki fada min ba?" Na sake sunkuyar da kaina nace "Daddy nima ban fara zargin shine ba sai bayan da muka dawo Nigeria, bayan da aka riga aka daura auren, Tun lokacin ya fara nuna min ya damu da abinda na haifa and I found that suspicious, Daga baya kuma saw some kind of resemblance tsakanin sada…...da.... Junior, Shine nace masa ya mutu, and he acted kamar uban da aka ce masa dan sa ya mutu" Daddy ya sake girgiza kai "but still you should have come to me ai. Da sai in dakatar da bikin in kashe auren in kuma bincike shi. Bai kamata ki saka kanki in danger ta hanyar tarewa a gidan sa alhalin kina zargin sa da wannan maganar ba. Zai iya yi miki komai dan ya rufa asirin kansa, zai iya daukar ranki ma. Akwai rapist da yawa da suke kashe victims din su dan gudun kar su tona musu asiri. Da kin gaya min sai mu tuhume shi in yaso in yaki sai mu dauko Junior ayi dna din, shikenan". Nayi shiru ina wasa da yatsun hannu na, ina jin kunyar Daddy sosai akan duk wata magana da ta shafi Junior, amma wannan magana ce da ya kamata muyi. Nace "Daddy I did all that for Junior. I was trying to avoid doing the DNA. Ina tsoron dna test din will blow off Junior's cover, Mukhtar zai san shi sauran yan'uwa zasu san shi, mutane zasu gane cewa ba dan Aunty Hajjo ba ne ba. I was trying to protect him from people and from the reality of his life. Na san zai sani watarana. Amma nati son in zai sani din ma sai ya zama strong enough to accept it, yadda ko ma me mutane zasu fada din ba zai affecting ginin rayuwarsa ba". Daddy yace "so you were trying to protect him by putting your own life in danger? By risking your life?" Na gyara zamana ina kallon sa nace "Ammie jumped to her death to protect me. She went through a lot of things dan taga na samu rayuwa mai kyau. Wannan shine version na motherhood da na sani. Wannan shine irin uwar da nake so in zama". And I saw him smile. It has been 20 years amma babu yadda za'a yi a ambaci sunan ta ba tare da zuciyar sa ta russuna ba. Babu yadda za'a yi ayi labarin ta ba tare da yayi murmushi ba. He said "shikenan. Allah ya bada sa'a yayi jagora. Allah kuma yayi miki albarka. Ahmad ya roka cewa a basu lokaci da Mukhtar, zamu jira shi muji abinda zai ce da kuma abinda zaiyi. Idan kuma bai yi abinda ya dace ba, mu zamu yi abinda ya dace". And then the waiting began ………. Muka fara zaman jiran hukuncin da Uncle Ahmad zai yanke, Kwana na uku a gida ranar nan muna zaune a falo da Mommy muna ta hirar twins and how they are coping with aikin su sai ga Safina ta shigo. Naji gabaki daya mood dina ya chanja. Har da gudun ta taje ta fada jikin Mommy tana murna. Mommy ta ture ta tana dariya. "ke dalla saukar min a jiki kar ki balla ni" Safina ta fara shagwaba "haba Mommy, na rame fa" Mommy ta kalle ta "kin rame tabbas amma yanxu ai naga kin fara dawo da jikin ki, kin murmure ba laifi. I guess your inlaws are treating you right ko?" Safina ya gyara zamanta sosai tana kallo na tace "suna da kirki sosai. Mama is the best mother in law in the whole world" Mommy tace "uhumm. Sai shine bashi da kirki kenan. Bai yi gadon halin kirki ba gaskiya" Safina ta bata rai "kai Mommy, baya... "Baya gari ne fa . " Mommy ta karasa tana kwaikwayon muryar ta. "Zancen kenan kullum baya gari. Ni ba zan ki fadar gaskiya ba fa. Mijin ki bashi da kirki. Ko a gaban sane ko a gaban iyayensa zan fada ballantana a gaban ki. Bashi da kirki ko kadan. Yanzu ji nake bikin Safiyya aka yi ko waya baiyi mana yace Allah ya sanya alkhairi ba ballantana ya kawo mana gudummawa. A haka kuma kullum kice wai aiki yayi masa yawa shi yasa baya zama a kasar, To ya dauke ki ya tafi da ke inda yake zuwa mana in da gaskiya ne……” Ta cigaba da wanke Muhammad ni dai na mayar da hankali na kan waya ta bance musu komai ba. Sai daga baya Safina ta mike ta ajiye mayafin ta tare da cewa "Mommy me kuke da shi abinci a gidan nan? Ina Esther take? Ta zo ta jefa min danwake, shi nake son ci da manja" Mommy tace "ke zauna tukuna ba maganar dan wake ake yi ba. Wai baki ga Safiyya ba? Ko bata baki labarin abinda yake faruwa ba? Ki zauna ki jajanta mata mana" Safina ta koma ta zauna tana kallona sannan tace "me ya faru?" Mommy ta fara bata labari "zancen cikin ta, ashe dai da na Mukhtar ne...." Ina jin su ta bata labari tiryan tiryan tun daga farko har karshe. Na lura da yadda yanayin fuskar safinan yake nuna tsananin tashin hankali, A karshe Mommy tace "to yanzu dai maganar da nake miki zaman jiran hukuncin da iyayenku maza zasu dauka muke yi. Bamu san dai abinda zasu ce ba amma abinda na tabbatar shine auren Safiyya da Mukhtar ya kare" Safina ta yi sauri ta kalle ni and I smiled brightly at her. Ta dafe kirji cikin tsananin tashin hankali "innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Hasbinallahu wa niimal wakel" Mommy tace "dole kiyi salati yar nan.. wannan abin tashin hankali ai ya kai inda ya kai. Sai dai kawai muyi mata addu'a Allah ya musanya mata da wanda ya fishi alkhairi" Safina ba ta yi magana ba sai ni nace "Amen Mommy. Nagode" Mommy ta mike, bara inje in gano ko baban ku ya tashi daga bacci in taimaka masa...." Ta cigaba da magana tana tafiya, tana fita na sake yiwa Safina murmushi "Hi dear sister.... Kinga ikon Allah ko? Har na kusa gamawa da dayan saura ke, ina gamawa da shi zan dawo kan ki kamar yadda nayi miki alkawari. I will not wait for karma to catch you. I will come for your head as soon as na gama da wancan munafikin. Kuma ba zan yi miki da sauki ba Safina, ke da kanki zaki ciro kan naki kiyi min serving din sa on a tray, You will regret sanda kika dora don ki a kan Muhammad". Tayi shiru tana kallo na, fuskar ta da idonta sunyi ja, ta bude baki amma ta kasa magana, daga dukkan alamu duk karerayin ta da mugayen maganganu ta sun kare, a karshe sai tace "he is my husband. And Daddy will never let you marry my husband and iyayen sa will never let him marry kanwar matar sa. Ballantana kuma someone with your reputation". Na mike tsaye ina kallon ta nace "har yanzu ko shekara ba'a yi ba da fara wannan dramar, and abubuwa da yawa sun faru most of which a shekarun baya nake kalla as impossible. Misali ke a matsayin matar Muhammad. Hakan yana nufin cewa God can change impossible to become possible through the most impossible way. Just wait and see, zaki sha mamaki. Ban san yadda abubuwa zasu kasance ba but na san cewa the moment da mijin ki yaji labarin aure na ya mutu he will run back to me as fast as his legs can carry him. And the rest will be history". Da niyyar kwana Safina tazo gidan amma bata iya kwanan ba, haka ta dauki mayafin ta ta dauki motar Mommy ta tafi da ita. Yanayin ta gabaki daya ya koma tamkar wadda aka cewa Mommy ta mutu, ita Mommy duk ta dauka labarin abinda ya fari da nine yayi affecting dinta hakan bata san ita Safina abinda ya faru da ni ko a jikinta ba dan ko jajanta min bata yi ba, ita tsoron ta kawai shine zan kwace mata mijinta. Ni kuma a lokacin ba zan ce Muhammad baya gaba na ba, dan in nace bana son sa nayi karya, amma na fadawa Safina wadancan maganganun ne dan in bata mata rai. Amma ni kaina na san akwai obstacles da yawa a tsakanin mu. Daga nan na cigaba da zaman jiran hukuncin da za'a yanke, ko dan ance aski in yazo gaban goshi yafi zafi? Sai naji yanzu nafi damuwa akan duk dadewar da nayi ina jiran bayyanar gaskiya. Mukhtar da yake kunya bata ishe shi ba haka yayi ta zabga min kira da messages a waya akan wai yana son muyi magana, naki kula shi sam, nayi blocking kiran sa na bar messages din duk wanda ya turo sai inyi screenshotting in ajiye ko zasu zamar min evidence. A haka har na kwana biyar a gida. Ranar ne ina zaune a dakina ina aiki akan system kawai naji an bude dakin an shigo sannan an mayar da kofar an rufe, na san mutum daya ne yake yi min hakan amma kuma ranar na san bashi ba ne ba, na juyo da sauri sai naga Mukhtar a tsaye ya jingina da jikin kofar yana kallo na. Kallo daya zakayi masa kasan cewa rayuwar sa gabaki daya a upside down take. Nayi sauri na saka hannu na a kasan gado inda nayi ajjiyar sabuwar wuka ta musamman saboda Mustapha, na juyo na nuna shi da ita nace "fita, ko a fitar da gawar ka" maimakon ya fita sai ya zame ya zauna a wajen yace "kill me, idan hakan shine abinda kike bukata" na karaso na tsaya a gabansa fuskata cike da tsanarsa hannu na rike da wukar nace "zan kashe ka wallahi, in kashe banza a banza kuma babu abinda za'a yi min". Yace "zaki iya yin hakan. Ko kuma zaki iya tsayawa ki saurare ni. Wata kila mu samar da mafita a cikin maganar da zamuyi" nace "bana bukatar wata mafita wadda ta shafe ka. I already know what I want kuma shine abinda zan samu. I want to see you locked up in prison for as long as possible" ya dago ido yana kallo na, fuskarsa kamar ba ta Mukhtar din da na sani ba. Yace "I don't care about going to prison Safiyya. I care about more important things than my freedom" nayi shiru ban ce komai ba, trying to control my heart da take zugani a kan in soka masa wukar hannu na, Ya cigaba "Umma ta fadi, tana asibiti kwanan ta biyu bata san waye a kanta ba. Abba yace babu shi babu ni har abada, And you" Cikin tsawa nace "don't talk about me. Kar inji sunana a cikin bakin ka. I don't care me iyayen ka suke ciki ko me suka yi maka. Ni ka damu da halin da nawa iyayen suka shiga a sanadin abinda kayi min? a damu da halin da na shiga a saboda abinda kayi min? Ka cuce ni Mukhtar! Ka cuce ni! Kayi min cuta ta har abada. Allah ya isa! Allah ya isa! Allah ya isa tsakani na da kai". Na fada ina kukan da har sai da wukar ya fadi daga hannu na. Ya kife fuskarsa akan guiwar sa yana kuka shima, jikinsa har rawa yake yi. Na zauna a kasa nima na jingina da jikin gado ina jin wani tarin tsanarsa tana kara yawa a zuciya ta. Gani nake yi da ace Mustapha ne yayi min wannan abun da ba zan tsane shi kamar yadda na tsani Mukhtar a yanzu ba. Ya dago fuskar sa yana kallo na yace " want to confess a gaban iyayen mu su yanke min hukuncin da zasu yanke min, but before then I want to tell you why I did it" nace "I don't want to know, I don't care" Yace "I know. But I want to tell you anyway. I did it because I love you. Ban taba son wani abu ba a duniya kamar Manna nake con ki Safivva Tin kina taba son wani abu ba a duniya kamar yadda nake son ki Safiyya. Tun kina karama nake sonki. I tried duk yadda zanyi inga kin so ni amma kika ki, babu yadda banyi ba, ke ma kin san babu yadda banyi ba. I even tried involving iyayen mu amma Daddy ya goyi bayan ki. Meanwhile you got some guy and you kept rubbing him on my face. I wanted to have you. I wanted you so bad...." Ya fada miko hannunsa zuwa gare ni, na janye jikina out of his reach nace "in ka sake ta bani sai na cire hannun ka. You are insane" ya ajiye hannun sa a gefe yace "I thought in na same ki ta wannan hanyar zan daina jin zafin soyayyar ki da take ci na. I thought in nayi miki haka maybe zaki rabu da wancan saurayin and might consider me. I thought maybe in iyayen mu suka fahimci abinda ya faru they might consider aura min ke. I never thought you will get pregnant. I never thought anyone will notice. But believe me Safiyya wallahi I regretted it tun a lokacin, sharrin shaidan ne da sharrin zuciya ta da na kasa controlling a akan ki. Na kai ki gida and I watched you har kika shiga gidan, thinking za'a yi miki fada ne kawai for staying out late and shikenan", Yayi shiru, maybe jira yake inyi magana, jin bani da niyyar yi sai ya cigaba "I was wrong. Maimakon abinda nayi ya rage min son ki da bukatar ki sai kara min ma da yayi. I waited inji kin rabu da wancan saurayin kinyi kokarin shiryawa da ni but you didn't. I thought kin manta ma da abinda ya faru and you have moved on, sai kuma ga kira daga asibiti that you went kina so zaki zubar da ciki, tun a lokacin na san cewa nawa ne. And I thought I hit the jackpot, nasan dole ki rabu da wancan saurayin naki and chances dina na auren ki ya karu. when you chose to marry me kuma sai naji kamar nafi kowa sa'a a duniya, I thought chance ne Allah ya bani na rectifying mistakes dina by taking care of you and abinda zaki haifa. Allah kuma sai ya saka min son sa shima a zuciya ta kamar yadda ya saka min ya kuma kara min naki. Ban san cewa tarkon kamani ne Allah ya dana min ba". Ya goge hawayen fuskarsa "I know all this doesn't matter. It doesn't change anything. Amma ina so ne kawai in gaya miki cewa I love you and I never meant to hurt you" idona yana rufe nace "and yet you did" yace "yes, amma nayi nadama tun a lokacin, you have no idea how it haunted me" na bude ido ina kallon sa nace "da kayi nadama da tun a lokacin you will turn yourself in, zaka kawo kanka gurin iyayen mu ko gurin hukuma ka nemi ayi maka hukunci. But you stood by and watched me suffer, hoping to have me again. No Mukhtar, ba ka yi nadama ba, not yet. I trusted you but You are just a selfish and entitled bastard with no single atom of imani a cikin zuciyarka. Your reason, duk a wadannan maganganun naka is just cewa kana so na, and who told you dan kace kana sona sai nima lallai na so ka? And let me tell you, ka cire kalmar so daga bakin ka. Kai baka sona, baka sona ko kadan. Ni na san menene so and it neither look nor sound like what you just described" Na gyara zamana nace "ina da wanda nake so kuma yake so na. And what I did sanda wanna musibar ta same ni shine na rabu da shi duk kuwa da son da nake yi masa, saboda na san cigaba da kasancewa tare da shi zai shafa masa bakin fentin da maybe har abada ba zai ¡ya goguwa ba. Babu abinda Daddy bai yi min ba, amma naki ko da kuwa ambatar sunan sa, duk kuwa da nasan maybe da na ambaci sunan na sa da yanzu ina gidan sa a matsayin matar sa. But I couldn't hurt him that way, I can never hurt him in any way because I love him. Wannan shine love" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya😥❤️‍🩹 Episode Forty Six: Decision Making Na tashi na koma inda nake zaune kafin ya shigo na zauna sannan nace "idan ka gama maganar da zaka yi ka kuma gama kukan zaka ¡ya fita" nayi kamar na cigaba da aikin da nake yi a system. Ya jima a gurin a zaune sai kuma ya mike yace "I know you have recorded all that I said, kamar yadda na san kinyi screenshot na messages dina, but you won't need them. Kamar yadda na gaya miki I am going to confess, ba kya bukatar wadansu shaidu tunda zan amsa laifina da bakina. Amma abu daya ne ba zanyi ba Safiyya, abu daya ne ba zan iya yi ba. Ba zan iya rabuwa da ke ba. You and my son are mine". Naji kamar ya soki zuciya ta na mike "your what? Did you just say your son?" Ya daga kafada "Allah ne kadai yasan dalilin da ya sa yaron ya zo duniya but I am greatful for him, maybe a saboda shi you will learn to love me, maybe he is meant to bring us back together" Na nuna shi da hannu nace "don't you ever call him your son again. Ba dan ka bane ba, ba shi da hadi in whatever way da kai. And I will never like you ballantana love, da da nake maka kallon mutumin kirki ma ban so ka ba Mukhtar ballantana yanzu da na san the kind of monster that you are? Get out of my room tun kafin in tara maka mutanen gidan nan". Ya bude kofa sannan ya sake juyo wa yana kallo na. Na fahimci maganar yake so ya cigaba sai na juya na shige toilet na rufe kofa. Na zauna dirshan a cikin toilet din na jingina da jikin bango, zuciya ta tana yi min zafin ambatar Junior as son da Mukhtar yayi. In da ace zan samu yadda nake so Mukhtar will never lay his eyes on Junior har karshen rayuwarsa. Sai da na tabbatar ya tafi sannan na fito, na sauka kasa muka ci abinci tare da Mommy, na lura ba ta san Mukhtar yazo ba dan da ta sani zata yi min maganar, Mustapha yazo shima ya zuba abincin yana ci suna magana da Mommy akan wadansu abokan babansa an siyasa da ya kaiwa takardun sa zasu sama masa aiki. Sai da suka gama maganar su ta tashi sannan yace min "can I kill him now?" Na girgiza kaina "not yet. Saura kadan" yayi ajiyar zuciya "I don't even know why I am listening to you, you of all people, after wulakancin da kika yi min a gidan nan" na juya ina kallon sa nace 'I thought you said you wanted to make it up to me?" Ya mike tsaye ya saka hannu a aljihu yace "yes, I want to do something for you dan in gyara tsakanin mu and dan in yi making up for my mistakes, but case din that bastard is my case dan haka babu ke a ciki. Kawai na baki time da shi ne out of the goodness of my heart, amma sai ya raina kansa wallahi, he tried to frame me Allah ne ya kare ni. I will return the favor to him, ni kuma in na haka masa nawa ramin muguntar ba zan jira shi ya fada ba ni zan je in hankada shi da kaina". Nayi murmushi bance komai ba sai ya juya zai fita. Na mike tsaye na kira sunan sa ya tsaya yana kallona, na je gabansa na tsaya nace "in har da gaske kana son gyara tsakanin mu then accept the job I offered you. Let's work together and take care of our parents" yace "so that ki samu damar yi min gori with every opportunity da kika samu?" Nace "in kace haka ba kayi min adalci ba, when na taba yi maka or anyone a gidan nan gori?" Ya danyi shiru sannan yace "I will think about it" nayi masa murmushi "that will be good" Mommy ta fito daga hanyar kitchen sai kuma ta tsaya tana kallon mu, Mustapha ya juya da sauri ya fita ni kuma na dawo cikin falo, na lura da yadda farin ciki ya cika fuskarta and I hoped 'she is not thinking what I think she is thinking' Sai da nayi sati daya a gida sannan uncle Ahmad ya dawo. Ranar da yazo ina kitchen naje zan dauko ruwa in sha naji muryarsa ya shigo gidan, sai nayi zama na a kitchen din naki fitowa har sai da Esther ta shigo tace Mommy tazo tana nemana wai in je inji Daddy, Na koma sama na dauko hijab na saka sannan na tafi falon Daddy, Ina shiga na gansu gabaki daya kamar ranar nan, Umma ce kadai babu. Na je in da na zauna ranar nan na sake zama nayi shiru, yau ma ban gaishe da kowa ba. Uncle Ahmad ya danyi gyaran murya sannan ya fara magana a hankali, na lura yayi loosing duk zafin kansa da takamar sa. Yace "ban san abinda zan fara fada a wannan zaman ba, kawai dai na san ni ne ya kamata in fara magana a matsayi na na baban ku gabaki daya. Musamman tunda yaya bashi da lafiya. Amma abinda na sani shine nayi nadama babba a rayuwata, nadamar da nayi kuwa ita ce ta haihuwar ka Mukhtar " ya fada yana nuna Mukhtar "da nasan wanna ranar zata zo min da ma shake ka tun kana jariri ka bar duniya dan ubanka" Ya karasa maganar cikin daga murya, na kalli Mukhtar na ga yadda ya takure a waje daya fuskarsa tana kallon kasa, and I wondered me yasa yazo gurin. Mommy tace "babu zancen yin dna test din kenan? Har na fara binciken asibitin da suka kware a wanna bangaren" Uncle Ahmad ya juyo yana kallon ta yace "na san farin ciki kike yi da wannan maganar, wannan kuma ya kara tabbatar min da who you really are. Wannan maganar ba abin murna ba ce ba. Abinda ya kamata mu zauna gabaki daya mu jajanta sannan mu nemi mafita akai ce" Mommy tace "wancan satin da aka zauna ai baka jajanta ba. Kin yarda ma kayi. Ka fara kokarin kare dan ka. Kuma ni ba murna nake yi ba amma bana jajantawa, na riga na jajanta na kuma zubar da hawayena tun a lokacin da aka zalunci yarinya, yanzu kuma da lokacin karbar mata hakkin ta yayi in banyi murna ba ma ai ba zan jajanta ba" Yace "babu wanda yafi karfin kaddara ta saukar masa..... Mommy tace "Allah ya raba mu da mummunar kaddara...”” Daddy yayi gyaran murya yace "yanzu menene abinda kazo zaka ce Ahmad? Kace a baka lokaci da yaro zaka tuhume shi kaji gaskiyar magana da ga bakin sa. Mun baka lokaci. Ka dawo. Fada mana abinda ka jiyo daga bakin nasa" uncle Ahmad yace "ni dai godiya daya da zan yi wa Allah a cikin wanna maganar ita ce da ya azurtani da wadansu yayan bayan Mukhtar, ina kuma saka ran insha Allah Allah ba zai hada min lalatattun yara irin sa ba" ya juya yana kallon Daddy yace "yaya, Mukhtar ya fada min da bakin sa cewa ya aikata laifin da yarinyar nan ta ce yayi. Mukhtar ne yay'" ya fadi maganar kamar zai yi kuka, Sai kuma yayi shiru yana kokarin daidaita muryar sa sannan yace "farko na ce masa babu ni babu shi har abada, sannan kuma kunyar ka da kuma kunyar yarinyar nan ta hana ni zuwa in gaya muku abinda ya ce min din. Amma kuma yanzu sai naga rashin zuwan nawa kamar kara wa laifina girma zaiyi a gurin ka. Kai yaya na ne, duk duniya bani da kamar ka". Ya sake juyawa wajen Daddy "yaya, dan Allah, kayi hakuri ya yafe min" Daddy bai ce komai ba yana dai kallon sa amma yanayin fuskar sa yana nuna tashin hankali da rudanin da zuciyar sa take ciki. Uncle Ahmad ya cigaba "yaya ka yafe min dan Allah. Ba wai Mukhtar nake nema wa yafiya a gurin ka ba dan nasan abinda yayi abu ne da zai yi wahalar a yafe masa lokaci daya, ni nake nema wa kaina yafiya a gurin ka saboda na gaza gurin tarbiyyar yaron nan. Amma Allah shine shaidata kuma kuma zaku iya zamar min shaida ko a lahira ne. Nayi iyakacin kokari na gurin tarbiyyar yaron nan" yayi shiru yana mayar da numfashi sannan ya cigaba "da nace babu ni babu shi har abada, amma kuma sai na ga hakan ba zai cire jini na daga jikin sa ba, Idan har zai iya aikawa wanna mummunan abun alhalin yana tare da mu me zai hana shi aikata abin da yafi wannan muni idan baya tare da mu?" "Gashi nan yaya na kawo maka shi. Kayi masa duk hukuncin da kake gain ya dace da shi". Falon yayi shiru, sai zuwa can Mommy tayi magana "chafi. Lallai duniya ta zama abin toro. Wai dan uwanka shi zai vi maka wannan cin mutuncin". Aka sake yin shiru zuwa can sannan Daddy yace "Mukhtar"' Mukhtar yayi shiru bai amsa ba. Kamar wanda yake kokarin shigewa cikin kujerar da yake zaune a gabanta. Daddy ya sake cewa "Mukhtar kai ne ka aikata wanna mummunan aikin? Kai ka cutar da kanwar ka Safiyya irin wannan cutarwar mai girma?" Mukhtar ya sake yin shiru bai yi magana ba. Daddy yayi kamar zai tashi daga kan kujerar sa cikin tsawa yace "answer me!" Mukhtar ya dago kai sannan ya fara jan guiwarsa zuwa gaban Daddy "Daddy dan Allah kayi hakuri.. Wallahi ina son ta ne....…. Wallah sharrin shaidan ne..........Ina sonta ne bana son in rasa ta, Dan Allah Daddy kayi hakuri ka yafe min". Daddy ya koma ya zauna yana kallon sa yace "kana son ta kake ce min Mukhtar..... Kayi mata wannan wulakancin sannan kace kana son ta? A haka ake soyayyar? An taba yin soyayya dole ne?" Mommy tace "zancen soyayya ma bata taso ba. Baka son ta Mukhtar ko kadan ba ka son yarinyar nan. Dan ko makiyin ka sai wanda kiyayyar tayi zurfi sannan zai iya aikata maka wanna mummunan abu. Karya kake yi wallahi Mukhtar" ya juyo gurinta "Wallahi Mommy da gaske nake.... Wallahi ina son ta. Tun tana karama nake son ta ita kuma tace bata so na" Mommy tace "tun tana karama? Kace Allah ne ya kiyaye mu da tun tana karama zaka aikata mata wannan aikin kenan tunda kai irin version of soyayyar ka kenan. To wannan ba soyayya bace ba bari kaji in gaya maka. Wannan sha'awa ce. Mummunar sha'awa ma kuwa irin mai cutarwar nan. Inda auren ya dore ma akwai yiyuwar zaka cigaba ne da cutar da ita kana kuma cigaba da gaya mata kalmar so, wannan shi ake kira da toxic love. Yanzu kuwa tunda Allah ya toni asirin ka mun gane halin ka to sai dai ka ci kanka ka sha bakin ruwa. Wannan yarinyar kai da ita sai hange daga nesa. Kai daga nesan ma ba zaka ganta ba". Mukhtar ya cigaba da kneeling a gaban Daddy, "Daddy dan Allah kayi magana, Wallahi nayi nadama" ya fada tare da fashewa da kuka, Still Daddy bai ce komai ba, Mommy tace "nadama tukunna Mukhtar. Baka yi nadama ba zaka yi dai", Uncle Ahmad yace "na yarda da ke a wannan karon. Nadama ai ba yanzu zaka yi ta ba tukunna. Kuma wannan kukan munafunci kake yi bana gaskiya ba. Kar kuma ka dora wa shaidan, sharrin zuciyar ka ne kawai da ka saka mata tunane tunane marasa kyau a cikin ta. Kuma shi da kake bawa hakuri ai ba shine wanda kayi wa laifin direct ba. Ga wacce kayi wa laifi can kaje ka durkusa ka bata hakuri". Mukhtar ya tashi daga gaban Daddy ya dawo gabana ya durkusa "Safiyya, na san na cutar da ke cuta mai girma. Na san nayi miki laifin da babu abinda zai taba goge miki shi daga cikin zuciyar ki. Amma wallahi nayi nadama. Dama kawai nake so a bani in gyara kurakurai na. Safiyya dan girman Allah da soyayyar da kike yiwa annabin rahama kiyi hakuri ki yafe min" Mommy tace "Sallallahu alaihi Wasallama". Ban dago kai na kalle shi ba ballantana inyi magana. Uncle Ahmad yace "to alhamdulillah. Sai ka godewa Allah tunda ya baka ikon neman yafiyar ta tun kuna da rai duk ku biyun. Dan Allah baya taba yafe laifin da akayi wa wani har sai in shi wanin ya yafe da kansa" sai kuma ya juya gurin Daddy yace "yanzu dai yaya da Mukhtar nan da Safiyya, dukkan su yayan ka ne. Ka yanke hukuncin duk da kake ganin ya dace da abinda ya faru a tsakanin su". Daddy ya danyi shiru yana bin mu da kallo sannan yace "yanzu Ahmad misali ace na bar maka wannan hukuncin. Nace ka yanke duk abinda kake gain shine dai dai. Me zaka yanke a kai?" Uncle Ahmad ya juyo yana kallon mu daya bayan daya sannan ace "to yaya. Wannan dai wani lamari ne mai sarkakiya. Lamari ne da ya shafi mutuncin ba su kansu yaran ba har da mu har da sauran yanuwansu da kuma yayan da zadu haifa nan gaba. Mutunci dai Mukhtar ya riga ya zubar mana da shi, abinda ya rage mana shine mu tattara wanda ya rage mana mu cigaba da kare shi. Irin wannan idan ya faru ko da ba'a cikin dangi daya bane ba kokari ake yi a rufe dan kare martabar dukkan bangarori biyun. Abunda akanyi idan an samu yaro takadiri irin Mukhtar ya haikewa yarinya irin haka to sai a matsa masa akan ya aure ta dan a kare martabar ta, shi kuma a bashi damar gyara kuskuren sa. Ballantana kuma yanzu da ya kasance har da rabo a tsakanin su, dole in mun tashi yanke hukunci mu duba har shi yaron da aka haifa. Muyi kokarin kare mutuncin sa da kuma rufe wa mutane hanyar da aka bi aka same shi ta hanyar tabbatar da aure a tsakanin iyayen sa. To alhamdulillah a wannan case din already ma akwai aure a tsakanin su. Already ubangiji ya riga ya rufa asirin abin. Duk hukuncin da za'a yiwa Mukhtar ayi masa amma a shawarce Yaya abar auren da yake a tsakanin su dan kare martabar yarinyar da dan da ta haifa da kuma bawa Mukhtar shima damar gyara kuskuren da ya aikata. Wannan shine nawa hangen. Amma abinda kace duk shi za'a yi". Tunda ya fara magana zuciya ta take zafi, ikon Allah ne kawai ya saka banyi magana ba har yaje karshe. Sai nayi shiru ina jiran inji abinda Daddy zai ce, zuciya tana bugawa tana bugawa da kaifi ina tsoron kar Daddy ya goyi bayan maganganun uncle Ahmad dan it will break my heart to say no to him Sai naji yace "na gane maganar ka Ahmad. Kuma na fahimci manufar ka. Sannan na yarda kana da gaskiya, dan kusan abinda ake yi kenan a cikin mutanen mu idan aka samu issue irin wannan, kokari ake yi a binne dan a kare martabar iyalin. Sai dai kuma matsalar guda daya ita ce, Safiyya is not like all the other girls da ake yin hakan akan su". "Tun Safiyya tana yarinya, tun bayan rasuwar mahaifiyar ta, loka6da na fara bata tarbiyya. Kai da Sa'adatu da sauran mutane da yawa kun sha gaya min cewa tarbiyyar da na ke bata ba irin wadda aka saba yi a kasar hausa ba ce ba, kuna ganin kamar ina lalata tarbiyyar ta ne ta hanyar bata freedom, musamman freedom of speech. Kunce sai abinda take so nake yi mata bana tursasa ta akan abinda ni nake son tayi. To yau zan gaya muku dalili. Za kuma ku fahimci result din tarbiyyar tawa. Ina bawa Safiyya zabi ne akan duk abinda ya shafe ta komai kankantar sa saboda ina so ta koyi making decisions a rayuwar ta dan nasan zata fuskanci kalubale da yawa, duk da ban hango mata wanna masifar ba amma na san zata fuskanci kalubale da yawa kuma dole zata bukaci courage din saying yes or no as a final decision. Na san kuma ba zan zauna tare da ita ba har abada. A yanzu kuwa ku kan ku shaida ne cewa Safiyya doesn't need anybody to make her decisions for her. Namu shine mu bata shawara a matsayin mu na wadanda muka fita hangen nesa, But the final say is hers" ya juyo yana kallo na yace "Safiyya, Talk to us, Ga abinda Mukhtar yace ga kuma shawarar da uncle dinki ya bayar. Me kika ce" Na dago kaina for the first time sannan na gyara zamana ina kallon su daya bayan daya, na sauke ido na akan Mukhtar nace "Mukhtar. Naji ka bani hakuri. Amma kuma ban karba ba. Ba zan iya hakura ba. Mukhtar ba zan iya yafe maka ba har abada. Ko da nace na yafe maka to ka tabbatar karya nake yi maka". Ya fara matsowa zuwa gaba na "Safiyya please.….. dan Allah" na cigaba "Abu daya zaka yi min in yafe maka" da sauri yace "menene? Anything you want" nace "ka je ka kai kanka kotun musulunci a yanke maka hukuncin da addini ya tanadar wa duk wanda ya aikata irin laifin ka. Idan kayi haka zan yafe maka. Ubangijin ma zai yafe maka tsallake iyakarsa da kayi" nan take naga yanayin fuskarsa ya chanja, ya juya ya kalli mahaifinsa sannan ya sake juyowa ya kalle ni. Nayi murmushi "na san ba zaka je ba. Saboda kamar yadda Mommy ta fada nadamar karya ce kake yi. You just want to emotionally blackmail us and blame shaidan for your actions, you want to eat your cake and still have it. You want to just say sorry to me and shade fake tears and you expect everything to just disappear, Sai a dauke ni a mayar da ni dakin ka kamar wata unwanted akuya". Na juya gurin Uncle Ahmad nace "uncle I am not sorry for saying this, ba zan koma gidan Mukhtar ba. Ba zan cigaba da zaman aure da Mukhtar ba ko da kuwa shi kadai ne ya rage a matsayin namiji a duniya. Tabbas abinda ka fada shine abinda ake yi wa mata da yawa a kasar hausa. Namiji yay raping mace sannan ayi forcing dinta to leave with him a matsayin mij for the rest of her life. Wannan zalunci ne ba karami ba. I was raped. Ni nasan irin tsanar da nake ji a zuciya ta ta wanda yayi raping dina, dan haka na san yadda wadannan matan suke ji a zuciyar su a game da mazan da ake matsa musu suyi zaman aure da su. Amma suna yin shiru su zauna dan basu da bakin magana kamar yadda Daddy yace. They are just yes girls. They just do what they are told and live a miserable life cikin kunci zuciya, hatred toward their husbands da kuma cigaban cin zali daga mazajen na su. Dan duk namijin da zai iya raping yarinya to tabbas cikakken azzalumi ne, kuma chances are he will continue to rape her day after day a cikin rayuwar auren nasu, Chances are high that she will never know what true marriage really feels like. Ga raping, ga auren dole sannan ayi sentencing dinta to life time of torture. And all for the crime that she didn't commit. Amma shi wanda yayi laifin sai reward ma da aka bashi na auren ta, babu wani hukuncin da za'a yanke masa saboda a rufe maganar kar aji kunya". Na girgiza kaina "no. Not me. That will never happen to me. Not in thousand years...…." Na juya kan Mukhtar nace "na baka shawara naga baka yarda ba. Okay in ba zaka yi hakan ba kana da wani option din again. You will go to jail. You will go to jail for as long as its legally possible for someone with your crimes. You will never go free, ba yan'uwan ta ka ba ko uwa daya uba daya muke da kai. I will make an example of you Mukhtar, maybe sauran mutane zasu yi following, maybe sauran mata zasu fara breaking this chain of torture suna reporting mazaje masu irin halin ka". Ya fara girgiza kai "Safiyya dan Allah. Na baki hakuri fa Safiyya nine fa Mukhtar. Wallahi ban san maganar zata yi karfin haka ba" ya juya gurin su Daddy "Daddy dan Allah ka bata hakuri. Abba dan Allah ka saka baki, Wallahi nayi nadama, Wallahi ban san zata samu ciki har ta sha wannan wahalar ba" Mommy tace "Allah ne ai ya kama ka shi yasa ta samu cikin. Da babu cikin da maybe har abada babu wanda zai san abinda ya faru sai dai tayi ta rije bakin ciki a cikin zuciyar ta har mutuwar ta" na juyo ina kallon ta nace "yes Mommy. Na tabbatar akwai mata da yawa da aka taba raping amma har su mutu babu wanda zai san anyi, sai dai abun yayi ta cin su a zuciyoyin su saboda fadar ma ya zama abun kunya. In mace ta fada ita za'a vi wa tambarin while culprit din will be free, ko kuma ma ace sharri tayi masa" Na mike tsaye ina kallon Mukhtar da yake ta hada uban gumi nace "I will see you in court" na juya zan fita sai uncle Ahmad ya mike ya kira suna na "Safiyya!" Na juyo ina kallon sa idanu na a bushe "what about you? Idan kin kai maganar nan court dole sunan ki yana ciki, ke yanzu babbar mace ce a cikin al'umma dan haka sunan ki zai yi tambari. Yes, za'a yanke masa hukunci a rufe shi ke kuma sunan ki zai baci. Shin ba zaki yi considering wannan ba?" Na juyo na dawo tsakiyar dakin nace "suna? Wanne irin suna ne ya rage min uncle? Wanne bacin suna zanyi wanda yafi wanda nake ciki yanzu? Maybe maidan maganar ta fita cewa I was raped in samu sympathy na sensible mutane. mean cikin shege fa nayi uncle, I already have a bastard child uncle, wanne mutunci ne kuma ya rage min?" Na fada with raising anger. Mommy ta mike "still Safiyya…... Nima yanzu na fara goyon bayan uncle din ki. You still have your reputation to protect Fiyya. A yanzu babu wanda ya sani sai gidajen nan guda biyu. In kika fitar da magana kuwa duniya gaba-daya zata sani" nace "for how long Mommy? For how long maganar zata tsaya a tsakanin mu? Safina will say it the first chance she gets. And someday aure zai iya taso min a garin bincike wani da ya ga wani abu zai iya gaya wa wani shima ya gaya wa wanj and then everyone will know, abinda kuma zasu sani sannan zasu fada shine Safiyya Adam Muhammad tayi cikin shege. No body will mention sunan Mukhtar a ciki. All fingers will point at me. The innocent me" Na ga duk still sun cigaba da kallona, daga alama babu wanda yake goyon bayana a cikin su sai na juya daga hanyar zuwa cikin gida nayi hanyar waje., Mommy ta rike hijab dina, "ina zaki je kuma Safiyya? Kar ki fita a wannan yanayin" na juyo ina kallon ta nace "zanje gidan radio da television da duk wata media channel that I can get to, zan je in bada labarin how my cousin raped me, and how my family are trying to cover it up dan su "kare martaba' ta, martabar da already aka riga aka zubar min. And I am also going to write an article inyi publishing on the Internet, in saka sunana da nasa, in bada labarin abinda ya faru sannan inyi tagging all the humanitarian organization da zasu kwato min hakkin da kuke kokarin hana ni karba" A falon babu wanda yake zaune sai Daddy, daga dukkan alamu duk na hada musu zafi. Uncle Ahmad ya rike hannuna shima "Safiyya. Yata ki nutsu ki dawo ki zauna. We will talk about this. Zamu sake magana. We will find a way out kinji?". Mommy kuma tana cewa "ba dai jail kike so ya tafi ba? Zai je jail but don't go and publish your name a duniya.…...." Suna ta maganganun su naji Daddy ya kira sunana "Safiyya!" Ya juya ina kallon sa yace "ki koma gida, Zamu yi magana in an jima" na karbe hannaye na daga gurin su nayi hanyar cikin gida, sai kuma Daddy ya juya yana kallon su yana murmushi yace "na tabbatar yanzu kun fahimci abinda nake nufi, She can stand up for herself, Ba ta tsoron uban kowa. Yanzu bani da damuwa, Ko yau na mutu na san she will take care of herself". A ranar na zauna da daddare na rubuta labari na da duk abinda ya far da ni. Including names and places da komai. Banyi publishing ba amma sai a barshi sai naji abinda Daddy zai ce. Amma har cikin zuciya ta bana jin damuwa wai dan nayi publishing sunana a matsayin rape victim. Washegari da safe naje gaishe da Daddy sai yace in zauna zamuyi magana. Ina zaune har Mustapha ya gama taimaka masa yaci abinci sannan ya fita ya bamu guri Daddy yace "naji maganganun ki jiya" nayi shiru ina sauraron sa sai na ji shima yayi shiru. Nace "Daddy to me zaka ce akai?" Yace "I don't know Safiyya. Ni na san zafin da nake ji a zuciya ta a matsayina na mahaifin ki ballantana kuma ke da abin ya faru da ke. Kuma zan so ace Mukhtar ya samu hukunci wanda yafi kowanne hukunci tsanani akan abinda yayi miki. Zan ji dadi sosai idan hakan ta faru ko dan ya zama izna ga yan baya" nace "good, Then kana goyon bayan in shigar da kara court kenan?" Yace "yes, zan so hakan, Amma kamar yadda Ahmad yace what about you?" Na girgiza kaina "I don't care about me Daddy. I have no honor left. Bani da wani sauran mutuncin da zan kare " yace "kina da shi Safiyya. Kina da shi sosai. Idan kuma kamar yadda kika ce you don't care about yourself what about Junior? What about other children da muke saka ran zaki yi aure nan gaba ki haifa? What about their reputation?" Nayi shiru ina kallon sa ina jin raina yana baci sai ya cigaba "ke uwa ce Safiyya. Just last week kika zauna anan kike gaya min yadda kika saka rayuwar ki a danger to protect martabar Junior. In kika ce zaki watsa labarin nan a duniya kin zubar da waccan maganar kenan gabakidayan ta, duk abinda kika yi kinyi in vain. And not only him, yayan duk da zaki haifa nan gaba will also be tagged with that. Zaki haifi dan halak nan gaba amma mutane will also call him shege saboda basu san wanne ne shegen ba. They will tag all your children as bastard. Duk inda kika je kika boye Junior sai anje an binciko shi. Ba karamin aikin mutanen mu bane ba ki ga pictures din sa suna yawo a social media together with your story ko kuma ma a kara wata karyar akai". Naji hawaye yana bin fuska ta "to yanzu shikenan Daddy? Shikenan ba za'a hukunta Mukhtar ba" yace "za'a iya hukunta shi Safiyya. But bata hanyar da kika dauko ba" na share hawaye na nace "ta wacce hanyar to, Daddy me zan yi? Ya zanyi?" Ya daga kafada "I don't know, But I know something. Your mother is the smartest person I know when it comes to decision making. And you are smarter than her. You are her modern version. Na tabbatar you will make the smartest decision" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Seven : The Decision *Free baking master class* I'll be sharing delightfully delicious recipes including how to make soft and fluffy doughnut for *free* it's completely free A-Z Click the link below to join Females only https://chat.whatsapp.com/ DN5w2VPGPhE0gf3700F9k0 0704248974 Zan koyarda snacks kala 8 kyauta acikinsu akwai yadda zakiyi doughnut me laushi da dadi classes dinnam kyauta ne daga farko har karshe Danna wannam link kiyi joining Mata kawai Or contact 07042486974 To be added https://chat.whatsapp.com/ DN5w2VPGPhE0gf3700F9ko Safiyya..... Ranar kwana nayi banyi bacci ba ina saka da warwara, a fahimci abinda Daddy yake nufi, amma sai dai kuma fahimtar ta sa ta toshe min hanyar da na biyo kuma na kasa ganin wata hanyar da zata bulle da ni xuwa destination dina. Na tashi nayi sallah na gaya wa Allah bukata ta na roje shi ya bani mafita tunda dai ni bani da ita. Sai wajen asuba na kwanta akan sallayar nayi bacci, bayan anyi sallah na tashi nayi sallah sannan na koma kan gado na kwanta bacci mai nauyi ya dauke ni. Ban farka ba sai da rana tayi sosai. Na tashi nayi wanka na shirya ina jin kaina yana yi min ciwo duk kuwa da cewa nayi bacci mai nauyi amma na san damuwa ce ta saka min ciwon kan. Na dauko waya ta ina dubawa sai na ga sako daga Abdul yana yi min mitar bana neman su sai in sun neme ni "munyi fushi" ya turo tare da hoton Junior ya bata rai ya turo baki, Sai na samu kaina da yin dariya, He looks so cute and innocent and doesn't deserve all this, Na shafa fuskar sa ta cikin wayar sai nace a hankali "hey you, It is going to be okay. You are going to be okay, I promise" Nayi replying Abdul tare da tsokanar sa ina tambayar sa labarin amarya. Sai kuma na tashi na tafi part din Daddy dan gaishe shi. Ina shiga na tarar da shi a falon sa tare da Mustapha suna gwada wani machine da aka siyo masa da zai taimaka masa wajen zama da tashi ba tare da an rike shi ba. Na zauna a gefe ina kallon su. Mustapha might be a bad person but he takes care of Daddy and I am greatful to him for that. Sai da suka gama sannan na karasa gurin sa na gaishe shi sannan nace ' "sai yanzu na tashi. I slept in" ya zauna yana haki saboda movements din da yayi sannan yace min "maybe baki yi bacci da dare ba ne ba ko?" Na sunkuya da kai nace "haka ne Daddy. Ina ta tunani ne. I am still not sure what I will do" yace "kin ci abinci?" Na girgiza kai "no, shigowa nayi da ma mu gaisa sai inje inci abincin" yace "good. Sai kuma yayi shiru ya kwantar da kansa tare da rufe idonsa, Har na fara tunanin tashi ina gain maybe bacci ya dauke shi sai kuma na ga ya bude ido yana kallona yace "na taba baki labarin siblings din Ammien ki?" Na gyara zama, ina son labarin Ammie ko a gurin waye ballantana a gurin Daddy, A gurin sa da sauran mutane na hada labarin ta. Nace "wanne labarin da ga ciki? Na yadda suka yi sanadin rasuwar baba Hadiza da su Sauda ko kuma na yadda suka biyo ta nan suka takurawa rayuwar ta?" Ya girgiza kai yace "na abinda ya faru da su bayan rasuwar ta" nace "Daddy you never talk about anything related to rasuwar Ammie. Labaran ka duk na sanda tana raye ne ba ka taba bani labarin lokacin rasuwar ta ko abinda ya far bayan rasuwar tata ba". Yayi shiru yana kallon tv amma ba wai tvn yake kalla ba. Ya dan jima sannan yace "tabbas yan'uwa Safiya sun tsane ta ita da yan'uwan ta, tsanar da har ta kaisu ga aikata abubuwa da dama wadanda suka zama sanadiyyar da Safiya ta rasa kowa nata. Sannan kuma sai Allah ya daukaka ta fiye da yadda bata yi tunani ba, fiye da yadda suma ba su taba mafarki ba, and they came back, zuciyoyin su still cike da tsanar ta, they threatened her life, suka kira ta da juya, suka kuma bita da mugayen maganganu na sharri". "A lokacin a irin daukakar da Safiya take da shi idan da taga dama zsta iya batar da su a duniya baki daya, idan da taga dama zata iya kai su kara ta lissafo irin abubuwan da suka aikata mata and she can get a good lawyer da zai iya rufe mata duk wanda yake da hannu a cikin abinda ya same ta. But she didn't do that. She said sanda ta shiga gidan su yaga yadda Allah ya mayar da su ita kuma ta ga yadda Allah ya mayar da ita sai ta san cewa Allah has already fought her battle for her. Bata bukatar revenge. Ya riga yayi mata. Amma sai ta ja jikinta daga gare su dan gujewa sharrin su. Ko sanda suke zuwa gidan nan. A cikin gidan nan sun taba gaya mata ido da ido cewa tunda ita juya ce bata haihuwa suna jira be ta mutu su ci gadon ta. She could have sue them a lokacin, but she didn't. She said taga abinda Allah yay musu wancan karon, wanna karon ma shi take jira yayi mata komai. She just took some protective measures and leave them with God". "And then she died" "Washegarin da ta rasu suka zo gidan nan, Bus guda suka yo shata daga Kura suka taho mazan su da matan su, yara da manya, Sanda suka zo aka gaya min sai nace a barsu su shigo, Na saka aka basu dakuna biyu, maza aka basu daya a waje mata kuma aka basu daya a cikin gida, Amma tun a lokacin sai suka tayar da rigimar su dakunan ta suke so a bude musu a sama su a dakin ta zasu sauka. Lokacin kina ta koke koken ki na neman mahaifiyar ki Sa'adatu da sauran mutane suna ta fama da ke amma su ko a kin su. Hajiya ta san ba alkhairi ne ya kawo su ba dan haka ta hau saman ta rufe dakunan ta rike key a hannun ta. Shikenan sai rikici. Suka kafa maganganu na rashin mutunci da izgilanci suke yiwa Hajiya, Sa'adatu kuma da sauran mutane suka shiga ciki, sai rigima ta tashi a gidan gaisuwa" "Ni ina can ina cikin matsananciyar damuwar abinda ya faru naji hayaniya. Ina ji dama na san sune. Nan take na kira police suka zo suka kwashe su gabakidaya suka tafi dasu. Sai da suka kwana a can. Ahmad ne yayi ta zirga- zirga sannan daga baya nace a sake su amma kar su dawo min gida. Su barni inji da abinda yake damuna". "Suka tafi din, amma basu hakura ba ranar sadakar bakwai sai gasu sun dawo, Mutane sun taru ana yi mata sadaka da adduoin neman rahamar ubangiji amma tun daga bakin gate suka fara zage zage, wai suna so suga uban da zai hana su shiga gidan, ai gidan ma yanzu nasu ne, ai ance musu dama gidan tane kuma su ne magadan ta dan haka sun zo karbar gadon su. Har nayi niyyar sake kiran police sai Alhaji Nasir ya hana ni. Ya aika aka shigo da su ya zaunar da su yace su zauna avi mata addu'a tare da su sannan sai a saurari maganar da suka zo da ita". "Aka gama zaman addu'a aka tashi. Suka sake zama da Alhaji Nasiru suka gaya masa sun zone karbar dukiyar da ta mutu ta bari, har da list din su a hannu na abubuwan da aka gaya musu ta mallaka. Alhaji Nasiru ace babu komai dama ai shi gado Allah ya riga ya raba shi. Su je su samo malamin da zai raba gadon sai su zo a raba a basu. Suka ki tafiya, dan sunce ko kudin motar da zasu koma kura basu da shi jira suke sai an basu su samu na mota a ciki, Alhaji Salisu ya sama musu gurin zama, sannan ya nemo alkalin da zai raba gado ya kawo ya hada su dashi, sannan ni kuma aka ce in bayar da abinda ta bari wanda za'a raba". "Ban je gurin ba dama nace ba zan je ba, sai na tura barrister Umar da sauran lawyers din ta suke managing affairs dinta suka je, suka gabatar da lissafin abubuwan da ta mutu ta bari wadanda suke nata. Wadannan sun hada da wadansu daga cikin kayan sskawarta, sauran tarkacen irin na mata, da kuma kudin da yake cikin account din ta. Ko mota bata da ita. Nan take sabuwar rigima ta rikice dan ma Allah yasa na gaya wa barrister su tafi da security dan babu abinda ba zai iya faruwa ba. Ai kam dai ance Dauda wuka ya fitar yace sai ya illata barrister Umar". "Nan take suka shigar da kara Court akan an cinye musu gadon yar'uwar su data mutu ta bar musu. Zama daya aka yi wa shari'ar alkali ya kori karar tunda basu da hujjar cewa wadannan kadarori da suka lissafa nata ne. Dan ga takardu lawyers din mu sunje da su da suke nuna duk kadarorin nan naki ne ba nata bane ba. Daga nan suka sake kai kara kotun musulunci. Sunce waccan kotun kafurci ake yi a ciki. A wannan zaman court din ne naje, na kuma yiwa alkali bayanin duk abinda Safiya tayi sanda tana da rai kuma cikin koshin lafiyar ta. Ta baki kyautar komai da ta mallaka kuma ke ce kadai yar ta a duniya. Na kuma nuna masa abinda ta mutu ta bari a matsayin nata. Sannan nace ni da ke mun yate gadon Safiya, abinda ta bari din mun bar musu su rike" "A take alkali ya tabbatar musu da cewa Musulunci ya yarda da abinda Safiya tayi, dan haka abinda na nuna musu din shine kawai abinda za'a raba a matsayin gadon ta, sannan kuma yace ni da ke musulunci bai bamu damar cewa mun yafe gado ba, ba'a yafe gado, dole sai an bamu sai dai in an bamu mu bayar in bama so" "Still sai suka tayar da rigimar wai ai kayan sakawa kadai na fito da su banda kayan daki, su sun san cewa kowacce mace tana da kayan dakin ta a gidan mijinta dan haka sai na fito da su gado da kujeru da sauran su ai suma kayan ta ne. Ni kuma na san sanda na sayi gidan nan na saka aka zuba komai a cikin sa, tabbas safiya ta sai abubuwa itama amma ba ma zanniya ware abinda ta siya da wanda na siya ba dan haka nace su zo su dauka. Ahmad yana ta bala'i nace ya barsu suzo su dauka. Na zo gida na kwashe duk abinda na san mai daraja ne kuma ta baki tun tana da rai, irin su gwala-gwalai da manyan suturu da designer perfumes din ta duk na adana a bangare na, Duk abinda yake bangaren ta kuma nace azo a dauka, Hatta carpet da labule ba'a bari ba sai da suka cire, Hatta cutlary set sai da suka dauke daga kitchen. Cokali basu bari ba, Har da mugunta, abinda aka ga ba zai dauku ba sai a fasa shi. Ban ce komai ba dan ni ta kaina nake yi. Duniyar ma ta fita daga kaina ballantana kayan da suke cikin ta. Suka kai alkali aka yiwa kaya kudi aka fitar da nawa da naki sauran aka basu. Ni dai ban sake komawa court din ba. Abinda aka bamu ma nace da Ahmad yaje yayi sadaka da su Allah ya kai mata ladan kabarin ta. Daga lokacin naji gidan gabaki daya ya fita daga kaina ba zan iya cigaba da zama a cikin sa ba. It holds a lot of good and bad memories for the both of us dan kema a lokacin kamar kinfi kukan neman ta in muka shigo gidan. A lokacin ne na yanke hukunci komawa Kano da zama to ease the pain for us". Yayi shiru yana hutawa, idon sa yayi ja, har yanzu mutuwar Ammie tana damun sa sosai and I couldn't imagine going through the pain of loosing her at the same time kuma da wannan bacin ran na yan'uwan ta. Ga kuma ni da na saka shi a gaba da rigima kullum. Muka cigaba da yin shiru sannan nace "Daddy to ba ka gaya min ba" yace "ban gaya miki me ba?" Nace "sanda zaka fara magana kace zaka bani labarin abinda ya faru da su bayan rasuwar ta. Menene ya faru da su?" Ya dan yi gyaran murya yace "a labarin da aka bani, Tun a gaban alkalin da ya raba gadon suka fara rigima akan abinda aka basu, matan suna ta zabar kayan sakawa daga cikin kayan da suka samu. Sai babban su, Yaya Malam, ya kwace komai daga hannun kowa yace su bari sai sun je gida sai suyi nasu rabon. Ya dauko shatar motar diban kaya aka kwashe duk kayan aka zuba a ciki, cash din kuma ya karba ya rike a hannun sa, su kuma suka shiga mota suka koma Kura gabakidayan su" "Daga baya Jamilu dan marigayiya Hajiya Kyauta, shi yake bani labarin abinda ya faru da su. Yace bayan sun je gida suka yi ta jiran motar kaya tazo shiru shiru mota bata zo ba. Tun suna tunanin matsala motar ta samu a hanya har suka fara tuhumar yaya Malam akan inda kaya suka makale, da farko yayi ta basu uzurirruka masu cike da karaiyayi. Daga baya bayan an debi tsahon lokaci ba tare da kaya sun zo ba sai suka hada kai suka je gidan sa suka ritsa shi suka ce lallai sai ya fadi inda kaya suke, a nan ne yaga babu sarki sai Allah sai yace musu kaya dai ya siyar da su, kudin kuma ya biya lawyer din da ya dauka ya tsaya musu a court, kudin hannunsa kuma da su ya biya kudin shatar motar da suke je suka dawo da kuma motar da aka dauki kayan, Dan haka babu wani abu da ya rage wanda zai basu”. "Wannan maganar ta bata musu rai sosai, a take Dauda ya cire wuka ya soka wa yaya Malam a kahon zuci, a take ya fadi ya mutu, yan sanda kuna suka kama Dauda, bayan anyi shari'ar sa sai aka yanke masa hukuncin daurin rai da rai". Ya sake yin shiru yana kallon expression din fuska ta. Ban taba tunanin wannan ne abinda ya faru da su Dauda ba ban kuma taba damuwa da lallai sai na san wani abu a game da su ba. Lallai Allah mai yawan hikima ma a cikin dukkan al'amuran sa. Daddy yayi murmushi yana lura da yadda labarin ya taba ni sai yace "ina fatan kin gane abinda nake so ki fahimta a cikin wannan labarin. When you leave all your battles in God's hand, God will fight all your battles for you. Za kuma ki samu justice din da baki taba zata ba, justice din da in ke kika yi fighting battle din to ba zaki samu irin su ba. Na sunkuyar da kaina ban ce komai ba, Duk tunani na ya kara dagule wa. Har sai da nayi masa sallama zan tafi sai ya kira ni. Na juyo ina kallon sa sai yace "idan kina son zuwa kura ba zan hana ki ba, Duk da Safiya tace kar in barki ki je dan tana gudun kar su biyo ki da sharri kamar yadda suka yi mata. Amma ni ba zan hana ki ba. Saboda na yarda cewa ba duk aka taru aka zama daya ba. Ba duk yayan Alhaji Haladu ne tantirai ba, tabbas ba za'a rasa na gari a cikin su wadanda zaki ¡ya yin zumunci da su ba". Ranar haka na wuni da Ammie a cikin zuciyata. Naji ina ta missing dinta sosai. Da yamma sai na dauki mota na tafi gidan Hajiya, a duk sanda kewar mahaifiya ta ta dame ni gurin ta nake zuwa in ji sanyi a raina. Ai kuwa munsha hira sosai har saida bakina ya fara ciwo saboda dariya, ta kuma ii dadin zuwa na fiye da yadda nayi tunani. Da zan tafi sai ta bata rai "Adamu bai kyauta min ba, bayan ya dauke min Safiya ke ma kuma ya raba ni da ke" na dawo gaban ta na durkusa nace "Daddy bai raba mu ba Hajiya, abubuwa ne suka dan yi min yawa a yanzu. Idan komai ya warware zaki ke gani na sosai insha Allah" ta bata rai "kullum haka kuke cewa ai. Yaushe ne komai zai daidaita? Su fa matsalolin duniya ba sa kare wa Safiyya, in kin gama da wasu ma wasu ne zasu taso, Just seize your moments Safiyya, be happy when ever you can, Enjoy your life saboda ita kuruciya guda daya ce in ta tafi bata dawowa. Don't let anyone snatch away your youth and your happiness from you", Na zauna sosai ina kallon ta nace "kin san wani abu Hajiya? I think we need to spend more time together. Zan shirya mana zuwa Umrah insha Allah very soon daga ni sai ke. Muyi spending at least two weeks together muna ibada. It is going to be fun" Hajiya tayi murmushi tana jin dadi amma sai tace "ni ina zan iya zuwa Umrah da wannan kafar tawa Safiyya? Da yaya zanyi dawafin?" Nace "don't worry zan tura ki a kujerar guragu", Muka yi dariya tace "ai kuwa zanji dadi in hakan ta kasance. Dama nayi missing ka'aba sosai". A ranar da daddare na yanke hukuncin abinda zanyi, kamar yadda Hajiya ta bani shawara, ba zan bar kowa yayi snatching happiness dina from me ba, sannan kuma kamar yadda Daddy ya bani shawara I won't jeopardize the future of Junior and my unborn kids for vengeance. Sai dai ban yanke shawarar ba sai da na vi istikara nayi addu'a sosai akai. Sannan na gaya wa Daddy nace ya kira su uncle Ahmad su zomu sake zama. Ranar da suka zo da aka kira ni sai na shiga gurin na tsaya a bakin kofa ina kallon su, deciding a raina that that day is going to be the last day da zamu zauna meeting akan wannan issue din dan ma basu karbi hukunci na ba sai da su cigaba da yin meetings din su kadai ban da ni. Dana shiga sai na zamu kujera na zauna akai instead of kasan da nake zama. A raina ina hoping da saka glasses dina but I didn't because of Daddy. Umma ta samu zuwa ita ma yau, kana gain ta kasan ta sha jinya. Ban gaishe su ba ranar ita ma. Ina zama uncle Ahmad ya mike ya zo gaba na ya ajiye min wata farar takarda akan cinyata yace "my resignation letter, as you requested" sai naji raina yayi min babu dadi but i didn't let that distract me from abinda na saka a gaba na. Daddy yana kallona yace "kin ce Mukhtar yazo kina da magana da shi, gashi nan ya zo tare da mu bakidaya. Wacce maganar ce zaki yi?" Na gyara zamana na kalli Mukhtar da yake can gefe daya a zaune sai na dauko waya ta na nemo number din barrister Umar a kira shi tare da sakashi a speaker na kuma ajiye wayar a kan dan table din da yake gaba na, Bata jima tana ringing ba ya dauka, na gaishe shi ya amsa cikin kulawa, And then I said "barrister Umar, ranar nan kace min I can come to you whenever nake da any legal issue" yace "tabbas, duk matsalar da kike da ita data danganci law kiyi min magana, even if I cannot handle it I will guide you to the right channel" nace "good. Yanzu tambaya ce da ni. Ina so inji menene hukuncin rape a Nigeria" cikin nuna damuwa yace "rape kuma Safiyya? I hope you are okay?" Nace "I am fine barrister, we will discuss more on it if the need arises" Yace "Okay. It depends gaskiya. Ya danganta da circumstances da abin ya faru a ciki, ya kuma danganta da how good the lawyer representing the case is. But the minimum is 10 years. The maximum is life imprisonment. Ana iya yanke hukuncin kisa ma in some cases idan rape din yayi leading to death, especially of small children" nagyada kaina ina kallon Mukhtar wanda shima ni yake kallo fuskar sa cike da damuwa nace "okay na gane. Thank you. This rape case da yasa nayi maka wannan maganar bai yi leading to death ba, but it also involves kidnapping, drugging, torturing and then raping. How many years kake ganin za'a samu?" Ya danyi shiru sannan yace "gaskiya kin lissafa manya manyan criminal offenses, any of which babban offense ne. Like I said, it depends, but my guess is a minimum of 30 years and maximum of life imprisonment if the lawyer is good and akwai evidence sosai" nace "akwai evidence, plenty, I even have a recording of the culprit confessing the crimes and emotionally blackmailing the victim. And don't worry about the lawyer, I can get a SAN" ya danyi dariya "you are sounding so much like your mother. Of course you can get a SAN. And a SAN can get the culprit locked up for life" nace "good. Then we are getting a SAN" nayi kokarin katse kiran sai naji yace "I am worried about you Safiyya are you okay? Case din waye wannan?" Nace "Nagode barrister, and don't worry about me I am okay. Zamu yi magana later". Na katse kiran ina kallon su, trying to study them. Definitely Mukhtar da ¡yayensa sun tsorata, a raina nace "oh, kace kuma ba ka tsoron a rufe ka, mayaudari" ya gyara zama ya kai sau biyar, Umma ce ta fara magana "Safiyya, ni ban damu da rufe Mukhtar da zaki yi ko ma me zakiyi masa ba, amma idan kika fitar da maganar nan ba Mukhtar ka dai zata shafa ba har damu baki daya, har da kannen sa da basu ji ba basu gani ba, har da abinda kika haifa da abinda zaku haifa nan gaba. Martabar gidan gabaki daya zaki rusa. Wannan shine zai zama tambarin gidan nan na har abada. " na juya ina kallon ta nace "martabar gidan gabaki daya Mukhtar ya rusa a lokacin da ya aikata min abinda ya aikata. Dan haka shine da laifin ba ni ba" Mommy tace "haka ne, ni zan fi kowa ma son a rufe Mukhtar har tsahon ransa dan shi ba karamin mugun mutum bane ba amma ba shi zaki duba ba. Bamu zaki duba ba. Innocent yaron can zaki duba. Da kuma sauran yaran da zasu zo nan gaba. Think about it Safiyya" na gyara zama na nace "nayi tunani akan maganar Mommy, i have been thinking a lot about it. Na duba innocents din kamar yadda kika ce. Wannan shi yasa na kira ku yau a gaban ku zan bawa Mukhtar options. It is either this...." Na fada ina nuna waya ta, or two other things" Uncle Ahmad da sai a lokacin yayi magana yace "what other things?" Nace "na farko zai rubuta min takardar saki ya bani. Na biyu zamu yi signing wani contract ni da shi" duk suka yi shiru suna kallo na sai nace "Yes, i am my mother's daughter and I like signing legal contracts" uncle Ahmad ya sake tambaya "wacce irin contract ce?" Nace "farko I will report to my team of lawyers and informed them about what happened to me. Zan rubuta komai in basu cewa on so so date I was raped by an unknown person har ma kuma na samu ciki na haihu on so so date. I will give them the details of everything, Ba zasu shigar da kara ba tunda babu suspect. And then Mukhtar and I will sign a contract na cewa he will never look at me or my son ever again. Bana son ganin shi a ko da kilomita goma daga inda ni ko dana muke. Ballantana har ya bude baki ya kira shi da sunan dan sa. He is not his son. Ko a musulunci bashi da hadi whatsoever with him. A duk kuwa ranar da ya ambace shi a matsayin dansa, it means my lawyers will have a suspect and a take zasu shigar da kara and he will be sentenced probably for life kamar yadda kuka ji an fada yanzu. Ambatar yaron da sunan dansa yana nufin yayi confessing publicly to all the crimes da na lissafa. Wannan contract din zata zauna har bayan raina for as long as shi yana raye". Na juya na kalli Daddy and I saw him smiling. Na sake juyawa gurin su uncle Ahmad nace "wannan shine decision dina, at least maybe you will know that I did all I can to protect the dignity of the family, Ba kamar wasu ba", Na koma na jingina da bayan kujera ta ina kallon su. Like I expected, Mukhtar ya fara retaliating, "Abba wallahi ina sonta ba zan iya rabuwa da ita ba. Ni gwara a yanke min hukuncin, na yarda a rufe ni din. Ina son yaron shima... " Abba ya tashi ya wawwanke fuskar sa da mari, Umma ta kama fada ita ma, Mommy ma haka. I sat and watched… As ina kallon su sai na fara lisssafin roles din kowa a cikin su a kan wannan maganar. Mommy have stood as my mother tun ina yarinya but masifar son kudin ta ya saka har yanxu na kasa tantance gaskiyar son da take yi min. Son kudin ne ya saka tayi ta kokarin cusa min Mustapha a matsayin miji, har yanzu kuma na ga alamar ba ta hakura ba. Son kudin ne ya saka take prioritizing duk abinda ya shafe ni over even Daddy, tana ganin kamar hakan ne zai saka ko babu ran Daddy in cigaba da kulawa da su ita da yayan ta. Sai dai zuwa yanxu na tabbatar bata fa hannu akan abinda ya same ni, Umma have been good to me while growing up, tana bani kulawa dai dai gwargwado duk sanda naje gidan su hutu, A lokacin da na fara makaranta a nan Abuja ma da na zauna a gidan su ta bani kulawa sosai. Sannan lokacin da Mukhtar ya fara cewa yana so na ta nuna amincewar ta da maganar dan har irin alkunyar nan ta fara nuna min ta surukai. Da na ki karbar soyayyar sa, a bar gidan su, sai dangantakar mu ta ragu sosai and I did not blame her, babu uwar da zata so ace ba'a son danta. But I thought she will get over it with time. Sai kuma gani da ciki, cikin shege, and sai kuma na zabi Mukhtar din a matsayin wanda zan aura to cover the cikin shegen da nayi. I think kowacce uwa will do abinda Umma tavi ko ma fiye da haka. Na fahimce ta. Wannan kuma ya saka bani da grudges whatsoever on her. And then uncle Ahmad. Uncle Ahmad bayan Daddy bani da wani father figure kamar sa. Babu kuma wand aya hidimtawa dukiyar Ammie da Daddy kamar shi. He spent his entire life yana aiki a karkashin su though not free tunda duk abinda ya ke da shi daga gare su ne but he gave it his best, Ita kuma dukiya tana da zaki, mutane kadan ne zasu so rabuwa da ita bayan sun dauki shekaru suna juya ta. Wannan shi yasa ya nuna goyon bayan saga aure na da Mukhtar tun a karon farko, wannan kuma shi yasa har a last zaman da muka yi ya ke cigaba da kokarin cusa min Mukhtar din dan yana gain aure na da Mukhtar zai saka ya cigaba da juya dukiyar kuma ko babu ransa to dansa da jikokin sane akan dukiyar, in babu raina ma sune zasu gaje ni. Amma kuma bashi da hannu a cikin abinda Mukhtar din yayi. Nayi kokarin dawo da hankali na kansu, har lokacin suna ta tafka rigima da Mukhtar, na lura cewa ba karamin maruwa fuskar Mukhtar tayi a gurin Uncle Ahmad ba dan fuskar har tayi ja ta fara kumbura, amma da yake ba shi da kunya still bai yi shiru ba. Na juyar da kaina gefe na daina kallon su. Na dauka uncle Ahmad zai cig6da dagewa a kan abar aurena da Mukhtar, sai kuma na lura cewa yanzu ya fahimci hakan ba mai yiyuwa bane ba ya hakura. And by submitting his resignation letter yana nufin ya sallama komai ya kuma hakura da komai. Da gaske uncle Ahmad huce haushin sa yake yi akan Mukhtar, dan bayan marikan da yake zuba masa har da kafa ya saka ya ke dukan sa. Ni dai sai na mike tsaye nayi cikin gida na barsu anan. Na gama kuma da wannan shafin. Ban yafe wa Mukhtar ba kuma bana jin zan yafe masa. Amma na bar shi da Allah, na kuma san hukuncin da zai yanke masa yafi wanda alkali zai yanke masa idan na kai shi court. Maman Maama✍🏻 Ina yan soyayya? Next post zamu tabo muku Malam Muhammadun ku insha Allah. Allah ya sa kar ya bada ku kuma😅[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Seven : The Decision *Free baking master class* I'll be sharing delightfully delicious recipes including how to make soft and fluffy doughnut for *free* it's completely free A-Z Click the link below to join Females only https://chat.whatsapp.com/ DN5w2VPGPhE0gf3700F9k0 0704248974 Zan koyarda snacks kala 8 kyauta acikinsu akwai yadda zakiyi doughnut me laushi da dadi classes dinnam kyauta ne daga farko har karshe Danna wannam link kiyi joining Mata kawai Or contact 07042486974 To be added https://chat.whatsapp.com/ DN5w2VPGPhE0gf3700F9ko Safiyya..... Ranar kwana nayi banyi bacci ba ina saka da warwara, a fahimci abinda Daddy yake nufi, amma sai dai kuma fahimtar ta sa ta toshe min hanyar da na biyo kuma na kasa ganin wata hanyar da zata bulle da ni xuwa destination dina. Na tashi nayi sallah na gaya wa Allah bukata ta na roje shi ya bani mafita tunda dai ni bani da ita. Sai wajen asuba na kwanta akan sallayar nayi bacci, bayan anyi sallah na tashi nayi sallah sannan na koma kan gado na kwanta bacci mai nauyi ya dauke ni. Ban farka ba sai da rana tayi sosai. Na tashi nayi wanka na shirya ina jin kaina yana yi min ciwo duk kuwa da cewa nayi bacci mai nauyi amma na san damuwa ce ta saka min ciwon kan. Na dauko waya ta ina dubawa sai na ga sako daga Abdul yana yi min mitar bana neman su sai in sun neme ni "munyi fushi" ya turo tare da hoton Junior ya bata rai ya turo baki, Sai na samu kaina da yin dariya, He looks so cute and innocent and doesn't deserve all this, Na shafa fuskar sa ta cikin wayar sai nace a hankali "hey you, It is going to be okay. You are going to be okay, I promise" Nayi replying Abdul tare da tsokanar sa ina tambayar sa labarin amarya. Sai kuma na tashi na tafi part din Daddy dan gaishe shi. Ina shiga na tarar da shi a falon sa tare da Mustapha suna gwada wani machine da aka siyo masa da zai taimaka masa wajen zama da tashi ba tare da an rike shi ba. Na zauna a gefe ina kallon su. Mustapha might be a bad person but he takes care of Daddy and I am greatful to him for that. Sai da suka gama sannan na karasa gurin sa na gaishe shi sannan nace ' "sai yanzu na tashi. I slept in" ya zauna yana haki saboda movements din da yayi sannan yace min "maybe baki yi bacci da dare ba ne ba ko?" Na sunkuya da kai nace "haka ne Daddy. Ina ta tunani ne. I am still not sure what I will do" yace "kin ci abinci?" Na girgiza kai "no, shigowa nayi da ma mu gaisa sai inje inci abincin" yace "good. Sai kuma yayi shiru ya kwantar da kansa tare da rufe idonsa, Har na fara tunanin tashi ina gain maybe bacci ya dauke shi sai kuma na ga ya bude ido yana kallona yace "na taba baki labarin siblings din Ammien ki?" Na gyara zama, ina son labarin Ammie ko a gurin waye ballantana a gurin Daddy, A gurin sa da sauran mutane na hada labarin ta. Nace "wanne labarin da ga ciki? Na yadda suka yi sanadin rasuwar baba Hadiza da su Sauda ko kuma na yadda suka biyo ta nan suka takurawa rayuwar ta?" Ya girgiza kai yace "na abinda ya faru da su bayan rasuwar ta" nace "Daddy you never talk about anything related to rasuwar Ammie. Labaran ka duk na sanda tana raye ne ba ka taba bani labarin lokacin rasuwar ta ko abinda ya far bayan rasuwar tata ba". Yayi shiru yana kallon tv amma ba wai tvn yake kalla ba. Ya dan jima sannan yace "tabbas yan'uwa Safiya sun tsane ta ita da yan'uwan ta, tsanar da har ta kaisu ga aikata abubuwa da dama wadanda suka zama sanadiyyar da Safiya ta rasa kowa nata. Sannan kuma sai Allah ya daukaka ta fiye da yadda bata yi tunani ba, fiye da yadda suma ba su taba mafarki ba, and they came back, zuciyoyin su still cike da tsanar ta, they threatened her life, suka kira ta da juya, suka kuma bita da mugayen maganganu na sharri". "A lokacin a irin daukakar da Safiya take da shi idan da taga dama zsta iya batar da su a duniya baki daya, idan da taga dama zata iya kai su kara ta lissafo irin abubuwan da suka aikata mata and she can get a good lawyer da zai iya rufe mata duk wanda yake da hannu a cikin abinda ya same ta. But she didn't do that. She said sanda ta shiga gidan su yaga yadda Allah ya mayar da su ita kuma ta ga yadda Allah ya mayar da ita sai ta san cewa Allah has already fought her battle for her. Bata bukatar revenge. Ya riga yayi mata. Amma sai ta ja jikinta daga gare su dan gujewa sharrin su. Ko sanda suke zuwa gidan nan. A cikin gidan nan sun taba gaya mata ido da ido cewa tunda ita juya ce bata haihuwa suna jira be ta mutu su ci gadon ta. She could have sue them a lokacin, but she didn't. She said taga abinda Allah yay musu wancan karon, wanna karon ma shi take jira yayi mata komai. She just took some protective measures and leave them with God". "And then she died" "Washegarin da ta rasu suka zo gidan nan, Bus guda suka yo shata daga Kura suka taho mazan su da matan su, yara da manya, Sanda suka zo aka gaya min sai nace a barsu su shigo, Na saka aka basu dakuna biyu, maza aka basu daya a waje mata kuma aka basu daya a cikin gida, Amma tun a lokacin sai suka tayar da rigimar su dakunan ta suke so a bude musu a sama su a dakin ta zasu sauka. Lokacin kina ta koke koken ki na neman mahaifiyar ki Sa'adatu da sauran mutane suna ta fama da ke amma su ko a kin su. Hajiya ta san ba alkhairi ne ya kawo su ba dan haka ta hau saman ta rufe dakunan ta rike key a hannun ta. Shikenan sai rikici. Suka kafa maganganu na rashin mutunci da izgilanci suke yiwa Hajiya, Sa'adatu kuma da sauran mutane suka shiga ciki, sai rigima ta tashi a gidan gaisuwa" "Ni ina can ina cikin matsananciyar damuwar abinda ya faru naji hayaniya. Ina ji dama na san sune. Nan take na kira police suka zo suka kwashe su gabakidaya suka tafi dasu. Sai da suka kwana a can. Ahmad ne yayi ta zirga- zirga sannan daga baya nace a sake su amma kar su dawo min gida. Su barni inji da abinda yake damuna". "Suka tafi din, amma basu hakura ba ranar sadakar bakwai sai gasu sun dawo, Mutane sun taru ana yi mata sadaka da adduoin neman rahamar ubangiji amma tun daga bakin gate suka fara zage zage, wai suna so suga uban da zai hana su shiga gidan, ai gidan ma yanzu nasu ne, ai ance musu dama gidan tane kuma su ne magadan ta dan haka sun zo karbar gadon su. Har nayi niyyar sake kiran police sai Alhaji Nasir ya hana ni. Ya aika aka shigo da su ya zaunar da su yace su zauna avi mata addu'a tare da su sannan sai a saurari maganar da suka zo da ita". "Aka gama zaman addu'a aka tashi. Suka sake zama da Alhaji Nasiru suka gaya masa sun zone karbar dukiyar da ta mutu ta bari, har da list din su a hannu na abubuwan da aka gaya musu ta mallaka. Alhaji Nasiru ace babu komai dama ai shi gado Allah ya riga ya raba shi. Su je su samo malamin da zai raba gadon sai su zo a raba a basu. Suka ki tafiya, dan sunce ko kudin motar da zasu koma kura basu da shi jira suke sai an basu su samu na mota a ciki, Alhaji Salisu ya sama musu gurin zama, sannan ya nemo alkalin da zai raba gado ya kawo ya hada su dashi, sannan ni kuma aka ce in bayar da abinda ta bari wanda za'a raba". "Ban je gurin ba dama nace ba zan je ba, sai na tura barrister Umar da sauran lawyers din ta suke managing affairs dinta suka je, suka gabatar da lissafin abubuwan da ta mutu ta bari wadanda suke nata. Wadannan sun hada da wadansu daga cikin kayan sskawarta, sauran tarkacen irin na mata, da kuma kudin da yake cikin account din ta. Ko mota bata da ita. Nan take sabuwar rigima ta rikice dan ma Allah yasa na gaya wa barrister su tafi da security dan babu abinda ba zai iya faruwa ba. Ai kam dai ance Dauda wuka ya fitar yace sai ya illata barrister Umar". "Nan take suka shigar da kara Court akan an cinye musu gadon yar'uwar su data mutu ta bar musu. Zama daya aka yi wa shari'ar alkali ya kori karar tunda basu da hujjar cewa wadannan kadarori da suka lissafa nata ne. Dan ga takardu lawyers din mu sunje da su da suke nuna duk kadarorin nan naki ne ba nata bane ba. Daga nan suka sake kai kara kotun musulunci. Sunce waccan kotun kafurci ake yi a ciki. A wannan zaman court din ne naje, na kuma yiwa alkali bayanin duk abinda Safiya tayi sanda tana da rai kuma cikin koshin lafiyar ta. Ta baki kyautar komai da ta mallaka kuma ke ce kadai yar ta a duniya. Na kuma nuna masa abinda ta mutu ta bari a matsayin nata. Sannan nace ni da ke mun yate gadon Safiya, abinda ta bari din mun bar musu su rike" "A take alkali ya tabbatar musu da cewa Musulunci ya yarda da abinda Safiya tayi, dan haka abinda na nuna musu din shine kawai abinda za'a raba a matsayin gadon ta, sannan kuma yace ni da ke musulunci bai bamu damar cewa mun yafe gado ba, ba'a yafe gado, dole sai an bamu sai dai in an bamu mu bayar in bama so" "Still sai suka tayar da rigimar wai ai kayan sakawa kadai na fito da su banda kayan daki, su sun san cewa kowacce mace tana da kayan dakin ta a gidan mijinta dan haka sai na fito da su gado da kujeru da sauran su ai suma kayan ta ne. Ni kuma na san sanda na sayi gidan nan na saka aka zuba komai a cikin sa, tabbas safiya ta sai abubuwa itama amma ba ma zanniya ware abinda ta siya da wanda na siya ba dan haka nace su zo su dauka. Ahmad yana ta bala'i nace ya barsu suzo su dauka. Na zo gida na kwashe duk abinda na san mai daraja ne kuma ta baki tun tana da rai, irin su gwala-gwalai da manyan suturu da designer perfumes din ta duk na adana a bangare na, Duk abinda yake bangaren ta kuma nace azo a dauka, Hatta carpet da labule ba'a bari ba sai da suka cire, Hatta cutlary set sai da suka dauke daga kitchen. Cokali basu bari ba, Har da mugunta, abinda aka ga ba zai dauku ba sai a fasa shi. Ban ce komai ba dan ni ta kaina nake yi. Duniyar ma ta fita daga kaina ballantana kayan da suke cikin ta. Suka kai alkali aka yiwa kaya kudi aka fitar da nawa da naki sauran aka basu. Ni dai ban sake komawa court din ba. Abinda aka bamu ma nace da Ahmad yaje yayi sadaka da su Allah ya kai mata ladan kabarin ta. Daga lokacin naji gidan gabaki daya ya fita daga kaina ba zan iya cigaba da zama a cikin sa ba. It holds a lot of good and bad memories for the both of us dan kema a lokacin kamar kinfi kukan neman ta in muka shigo gidan. A lokacin ne na yanke hukunci komawa Kano da zama to ease the pain for us". Yayi shiru yana hutawa, idon sa yayi ja, har yanzu mutuwar Ammie tana damun sa sosai and I couldn't imagine going through the pain of loosing her at the same time kuma da wannan bacin ran na yan'uwan ta. Ga kuma ni da na saka shi a gaba da rigima kullum. Muka cigaba da yin shiru sannan nace "Daddy to ba ka gaya min ba" yace "ban gaya miki me ba?" Nace "sanda zaka fara magana kace zaka bani labarin abinda ya faru da su bayan rasuwar ta. Menene ya faru da su?" Ya dan yi gyaran murya yace "a labarin da aka bani, Tun a gaban alkalin da ya raba gadon suka fara rigima akan abinda aka basu, matan suna ta zabar kayan sakawa daga cikin kayan da suka samu. Sai babban su, Yaya Malam, ya kwace komai daga hannun kowa yace su bari sai sun je gida sai suyi nasu rabon. Ya dauko shatar motar diban kaya aka kwashe duk kayan aka zuba a ciki, cash din kuma ya karba ya rike a hannun sa, su kuma suka shiga mota suka koma Kura gabakidayan su" "Daga baya Jamilu dan marigayiya Hajiya Kyauta, shi yake bani labarin abinda ya faru da su. Yace bayan sun je gida suka yi ta jiran motar kaya tazo shiru shiru mota bata zo ba. Tun suna tunanin matsala motar ta samu a hanya har suka fara tuhumar yaya Malam akan inda kaya suka makale, da farko yayi ta basu uzurirruka masu cike da karaiyayi. Daga baya bayan an debi tsahon lokaci ba tare da kaya sun zo ba sai suka hada kai suka je gidan sa suka ritsa shi suka ce lallai sai ya fadi inda kaya suke, a nan ne yaga babu sarki sai Allah sai yace musu kaya dai ya siyar da su, kudin kuma ya biya lawyer din da ya dauka ya tsaya musu a court, kudin hannunsa kuma da su ya biya kudin shatar motar da suke je suka dawo da kuma motar da aka dauki kayan, Dan haka babu wani abu da ya rage wanda zai basu”. "Wannan maganar ta bata musu rai sosai, a take Dauda ya cire wuka ya soka wa yaya Malam a kahon zuci, a take ya fadi ya mutu, yan sanda kuna suka kama Dauda, bayan anyi shari'ar sa sai aka yanke masa hukuncin daurin rai da rai". Ya sake yin shiru yana kallon expression din fuska ta. Ban taba tunanin wannan ne abinda ya faru da su Dauda ba ban kuma taba damuwa da lallai sai na san wani abu a game da su ba. Lallai Allah mai yawan hikima ma a cikin dukkan al'amuran sa. Daddy yayi murmushi yana lura da yadda labarin ya taba ni sai yace "ina fatan kin gane abinda nake so ki fahimta a cikin wannan labarin. When you leave all your battles in God's hand, God will fight all your battles for you. Za kuma ki samu justice din da baki taba zata ba, justice din da in ke kika yi fighting battle din to ba zaki samu irin su ba. Na sunkuyar da kaina ban ce komai ba, Duk tunani na ya kara dagule wa. Har sai da nayi masa sallama zan tafi sai ya kira ni. Na juyo ina kallon sa sai yace "idan kina son zuwa kura ba zan hana ki ba, Duk da Safiya tace kar in barki ki je dan tana gudun kar su biyo ki da sharri kamar yadda suka yi mata. Amma ni ba zan hana ki ba. Saboda na yarda cewa ba duk aka taru aka zama daya ba. Ba duk yayan Alhaji Haladu ne tantirai ba, tabbas ba za'a rasa na gari a cikin su wadanda zaki ¡ya yin zumunci da su ba". Ranar haka na wuni da Ammie a cikin zuciyata. Naji ina ta missing dinta sosai. Da yamma sai na dauki mota na tafi gidan Hajiya, a duk sanda kewar mahaifiya ta ta dame ni gurin ta nake zuwa in ji sanyi a raina. Ai kuwa munsha hira sosai har saida bakina ya fara ciwo saboda dariya, ta kuma ii dadin zuwa na fiye da yadda nayi tunani. Da zan tafi sai ta bata rai "Adamu bai kyauta min ba, bayan ya dauke min Safiya ke ma kuma ya raba ni da ke" na dawo gaban ta na durkusa nace "Daddy bai raba mu ba Hajiya, abubuwa ne suka dan yi min yawa a yanzu. Idan komai ya warware zaki ke gani na sosai insha Allah" ta bata rai "kullum haka kuke cewa ai. Yaushe ne komai zai daidaita? Su fa matsalolin duniya ba sa kare wa Safiyya, in kin gama da wasu ma wasu ne zasu taso, Just seize your moments Safiyya, be happy when ever you can, Enjoy your life saboda ita kuruciya guda daya ce in ta tafi bata dawowa. Don't let anyone snatch away your youth and your happiness from you", Na zauna sosai ina kallon ta nace "kin san wani abu Hajiya? I think we need to spend more time together. Zan shirya mana zuwa Umrah insha Allah very soon daga ni sai ke. Muyi spending at least two weeks together muna ibada. It is going to be fun" Hajiya tayi murmushi tana jin dadi amma sai tace "ni ina zan iya zuwa Umrah da wannan kafar tawa Safiyya? Da yaya zanyi dawafin?" Nace "don't worry zan tura ki a kujerar guragu", Muka yi dariya tace "ai kuwa zanji dadi in hakan ta kasance. Dama nayi missing ka'aba sosai". A ranar da daddare na yanke hukuncin abinda zanyi, kamar yadda Hajiya ta bani shawara, ba zan bar kowa yayi snatching happiness dina from me ba, sannan kuma kamar yadda Daddy ya bani shawara I won't jeopardize the future of Junior and my unborn kids for vengeance. Sai dai ban yanke shawarar ba sai da na vi istikara nayi addu'a sosai akai. Sannan na gaya wa Daddy nace ya kira su uncle Ahmad su zomu sake zama. Ranar da suka zo da aka kira ni sai na shiga gurin na tsaya a bakin kofa ina kallon su, deciding a raina that that day is going to be the last day da zamu zauna meeting akan wannan issue din dan ma basu karbi hukunci na ba sai da su cigaba da yin meetings din su kadai ban da ni. Dana shiga sai na zamu kujera na zauna akai instead of kasan da nake zama. A raina ina hoping da saka glasses dina but I didn't because of Daddy. Umma ta samu zuwa ita ma yau, kana gain ta kasan ta sha jinya. Ban gaishe su ba ranar ita ma. Ina zama uncle Ahmad ya mike ya zo gaba na ya ajiye min wata farar takarda akan cinyata yace "my resignation letter, as you requested" sai naji raina yayi min babu dadi but i didn't let that distract me from abinda na saka a gaba na. Daddy yana kallona yace "kin ce Mukhtar yazo kina da magana da shi, gashi nan ya zo tare da mu bakidaya. Wacce maganar ce zaki yi?" Na gyara zamana na kalli Mukhtar da yake can gefe daya a zaune sai na dauko waya ta na nemo number din barrister Umar a kira shi tare da sakashi a speaker na kuma ajiye wayar a kan dan table din da yake gaba na, Bata jima tana ringing ba ya dauka, na gaishe shi ya amsa cikin kulawa, And then I said "barrister Umar, ranar nan kace min I can come to you whenever nake da any legal issue" yace "tabbas, duk matsalar da kike da ita data danganci law kiyi min magana, even if I cannot handle it I will guide you to the right channel" nace "good. Yanzu tambaya ce da ni. Ina so inji menene hukuncin rape a Nigeria" cikin nuna damuwa yace "rape kuma Safiyya? I hope you are okay?" Nace "I am fine barrister, we will discuss more on it if the need arises" Yace "Okay. It depends gaskiya. Ya danganta da circumstances da abin ya faru a ciki, ya kuma danganta da how good the lawyer representing the case is. But the minimum is 10 years. The maximum is life imprisonment. Ana iya yanke hukuncin kisa ma in some cases idan rape din yayi leading to death, especially of small children" nagyada kaina ina kallon Mukhtar wanda shima ni yake kallo fuskar sa cike da damuwa nace "okay na gane. Thank you. This rape case da yasa nayi maka wannan maganar bai yi leading to death ba, but it also involves kidnapping, drugging, torturing and then raping. How many years kake ganin za'a samu?" Ya danyi shiru sannan yace "gaskiya kin lissafa manya manyan criminal offenses, any of which babban offense ne. Like I said, it depends, but my guess is a minimum of 30 years and maximum of life imprisonment if the lawyer is good and akwai evidence sosai" nace "akwai evidence, plenty, I even have a recording of the culprit confessing the crimes and emotionally blackmailing the victim. And don't worry about the lawyer, I can get a SAN" ya danyi dariya "you are sounding so much like your mother. Of course you can get a SAN. And a SAN can get the culprit locked up for life" nace "good. Then we are getting a SAN" nayi kokarin katse kiran sai naji yace "I am worried about you Safiyya are you okay? Case din waye wannan?" Nace "Nagode barrister, and don't worry about me I am okay. Zamu yi magana later". Na katse kiran ina kallon su, trying to study them. Definitely Mukhtar da ¡yayensa sun tsorata, a raina nace "oh, kace kuma ba ka tsoron a rufe ka, mayaudari" ya gyara zama ya kai sau biyar, Umma ce ta fara magana "Safiyya, ni ban damu da rufe Mukhtar da zaki yi ko ma me zakiyi masa ba, amma idan kika fitar da maganar nan ba Mukhtar ka dai zata shafa ba har damu baki daya, har da kannen sa da basu ji ba basu gani ba, har da abinda kika haifa da abinda zaku haifa nan gaba. Martabar gidan gabaki daya zaki rusa. Wannan shine zai zama tambarin gidan nan na har abada. " na juya ina kallon ta nace "martabar gidan gabaki daya Mukhtar ya rusa a lokacin da ya aikata min abinda ya aikata. Dan haka shine da laifin ba ni ba" Mommy tace "haka ne, ni zan fi kowa ma son a rufe Mukhtar har tsahon ransa dan shi ba karamin mugun mutum bane ba amma ba shi zaki duba ba. Bamu zaki duba ba. Innocent yaron can zaki duba. Da kuma sauran yaran da zasu zo nan gaba. Think about it Safiyya" na gyara zama na nace "nayi tunani akan maganar Mommy, i have been thinking a lot about it. Na duba innocents din kamar yadda kika ce. Wannan shi yasa na kira ku yau a gaban ku zan bawa Mukhtar options. It is either this...." Na fada ina nuna waya ta, or two other things" Uncle Ahmad da sai a lokacin yayi magana yace "what other things?" Nace "na farko zai rubuta min takardar saki ya bani. Na biyu zamu yi signing wani contract ni da shi" duk suka yi shiru suna kallo na sai nace "Yes, i am my mother's daughter and I like signing legal contracts" uncle Ahmad ya sake tambaya "wacce irin contract ce?" Nace "farko I will report to my team of lawyers and informed them about what happened to me. Zan rubuta komai in basu cewa on so so date I was raped by an unknown person har ma kuma na samu ciki na haihu on so so date. I will give them the details of everything, Ba zasu shigar da kara ba tunda babu suspect. And then Mukhtar and I will sign a contract na cewa he will never look at me or my son ever again. Bana son ganin shi a ko da kilomita goma daga inda ni ko dana muke. Ballantana har ya bude baki ya kira shi da sunan dan sa. He is not his son. Ko a musulunci bashi da hadi whatsoever with him. A duk kuwa ranar da ya ambace shi a matsayin dansa, it means my lawyers will have a suspect and a take zasu shigar da kara and he will be sentenced probably for life kamar yadda kuka ji an fada yanzu. Ambatar yaron da sunan dansa yana nufin yayi confessing publicly to all the crimes da na lissafa. Wannan contract din zata zauna har bayan raina for as long as shi yana raye". Na juya na kalli Daddy and I saw him smiling. Na sake juyawa gurin su uncle Ahmad nace "wannan shine decision dina, at least maybe you will know that I did all I can to protect the dignity of the family, Ba kamar wasu ba", Na koma na jingina da bayan kujera ta ina kallon su. Like I expected, Mukhtar ya fara retaliating, "Abba wallahi ina sonta ba zan iya rabuwa da ita ba. Ni gwara a yanke min hukuncin, na yarda a rufe ni din. Ina son yaron shima... " Abba ya tashi ya wawwanke fuskar sa da mari, Umma ta kama fada ita ma, Mommy ma haka. I sat and watched… As ina kallon su sai na fara lisssafin roles din kowa a cikin su a kan wannan maganar. Mommy have stood as my mother tun ina yarinya but masifar son kudin ta ya saka har yanxu na kasa tantance gaskiyar son da take yi min. Son kudin ne ya saka tayi ta kokarin cusa min Mustapha a matsayin miji, har yanzu kuma na ga alamar ba ta hakura ba. Son kudin ne ya saka take prioritizing duk abinda ya shafe ni over even Daddy, tana ganin kamar hakan ne zai saka ko babu ran Daddy in cigaba da kulawa da su ita da yayan ta. Sai dai zuwa yanxu na tabbatar bata fa hannu akan abinda ya same ni, Umma have been good to me while growing up, tana bani kulawa dai dai gwargwado duk sanda naje gidan su hutu, A lokacin da na fara makaranta a nan Abuja ma da na zauna a gidan su ta bani kulawa sosai. Sannan lokacin da Mukhtar ya fara cewa yana so na ta nuna amincewar ta da maganar dan har irin alkunyar nan ta fara nuna min ta surukai. Da na ki karbar soyayyar sa, a bar gidan su, sai dangantakar mu ta ragu sosai and I did not blame her, babu uwar da zata so ace ba'a son danta. But I thought she will get over it with time. Sai kuma gani da ciki, cikin shege, and sai kuma na zabi Mukhtar din a matsayin wanda zan aura to cover the cikin shegen da nayi. I think kowacce uwa will do abinda Umma tavi ko ma fiye da haka. Na fahimce ta. Wannan kuma ya saka bani da grudges whatsoever on her. And then uncle Ahmad. Uncle Ahmad bayan Daddy bani da wani father figure kamar sa. Babu kuma wand aya hidimtawa dukiyar Ammie da Daddy kamar shi. He spent his entire life yana aiki a karkashin su though not free tunda duk abinda ya ke da shi daga gare su ne but he gave it his best, Ita kuma dukiya tana da zaki, mutane kadan ne zasu so rabuwa da ita bayan sun dauki shekaru suna juya ta. Wannan shi yasa ya nuna goyon bayan saga aure na da Mukhtar tun a karon farko, wannan kuma shi yasa har a last zaman da muka yi ya ke cigaba da kokarin cusa min Mukhtar din dan yana gain aure na da Mukhtar zai saka ya cigaba da juya dukiyar kuma ko babu ransa to dansa da jikokin sane akan dukiyar, in babu raina ma sune zasu gaje ni. Amma kuma bashi da hannu a cikin abinda Mukhtar din yayi. Nayi kokarin dawo da hankali na kansu, har lokacin suna ta tafka rigima da Mukhtar, na lura cewa ba karamin maruwa fuskar Mukhtar tayi a gurin Uncle Ahmad ba dan fuskar har tayi ja ta fara kumbura, amma da yake ba shi da kunya still bai yi shiru ba. Na juyar da kaina gefe na daina kallon su. Na dauka uncle Ahmad zai cig6da dagewa a kan abar aurena da Mukhtar, sai kuma na lura cewa yanzu ya fahimci hakan ba mai yiyuwa bane ba ya hakura. And by submitting his resignation letter yana nufin ya sallama komai ya kuma hakura da komai. Da gaske uncle Ahmad huce haushin sa yake yi akan Mukhtar, dan bayan marikan da yake zuba masa har da kafa ya saka ya ke dukan sa. Ni dai sai na mike tsaye nayi cikin gida na barsu anan. Na gama kuma da wannan shafin. Ban yafe wa Mukhtar ba kuma bana jin zan yafe masa. Amma na bar shi da Allah, na kuma san hukuncin da zai yanke masa yafi wanda alkali zai yanke masa idan na kai shi court. Maman Maama✍🏻 Ina yan soyayya? Next post zamu tabo muku Malam Muhammadun ku insha Allah. Allah ya sa kar ya bada ku kuma😅 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Eight: Busted! Not Edited and typed when tired😴, so expect a lot of typos Him👳🏻‍♀️ Duk da kokarin Gidado na ganin cewa ya dawo Nigeria da wuri amma hakan bai samu ba sai da ya yi wata uku da barin kasar, sai dai watan karshe yayi shine ba cikin kwanciyar hankali ba dan sam bai amince da idea din zaman Safina tare da mahaifan sa ba. Yasan yarinyar is very conniving and manipulative, yana tsoron sharrin ta. Dan haka lokacin da zai dawo din ma he tried to emotionally prepared himself for koma menene zai tarar a gidan. A ransa yayi ta lissafa scenarios, yana hasaso sharrin da Safina zata iya shirya masa a gurin iyayensa, duk yawancin tunanin sa akan Safiyya ne, gani yake zata iya creating karerayin da zasu kara bata Safiyya a wajen su Mama, dan yasan dai shi bata isa tayi masa karya a gurin ¡yayensa ba dan idan tayi ma tana yi zasu san karya take yi. And that would be the worst mistake ever da zata yi a rayuwar auren su. Ranar da zai zo already ya gaya wa Abba da Mama, ya san kuma zai samu tarba ta musamman daga Mama dan sai tambayar sa take yi wanne kalar abinci yafi missing tayi masa "ga Safina nan sai ta taya ni muyi maka" yaji abincin har ya fita daga kansa tun kafin a dafa shi yace "Mama yarinyar nan ba iya girki tayi ba, in kika bata zata bata min abinci ne" Mama tayi dariya "na sani. Bata iya girki ba but she is trying to learn, kusan kullum in ana abinci a gidan nan sai ta shiga kitchen ta zauna, kullum kuma tana tambayar abincin da kafi so tana mayar da hankali a kai. Dan dai ma bata da lafiya ne shi yasa dole ta hakura da shiga kitchen din" yayi shiru bai ce komai ba, shi baya son wannan zancen rashin lafiyar Safina da Mama take yi masa kullum, he doesn't want to talk about it, he doesn't want to think about it. Sai ta kara da cewa "yarinyar nan tana son ka Muhammad" ya chanja topic "ba sai kun aiko a dauko ni ba, muni magana da Ya Amen zai zo ya dauke ni". Har a jirgi lissafin abinda rayuwa tayi keeping in store for him a Nigeria yayi ta yi. Abinda ya riga yay coming in terms with shine the fact that soyayyar Safiyya ita ce jarabawar rayuwar sa, yana kuma iyakacin kokarin sa na ganin cewa ya ci wanna jarabawar. Kamar duk sanda ya hau jirgi, wannan karon ma sai da ya tuna da ranar da suka fara haduwa a jirgin, she was the most sweetest girl and he was just a teenager. There was nothing romantic about haduwar ta su but it was the most memorable thing about their relationship. Yana sauka ya fito daga jirgi hasken rana ya haske masa ido, ya daga hannu ya kare fuskarsa and again ita ce ta fado masa a rai with her collection of sun shades, a cikin jakarta a cikin motarta a ko'ina take ba ka raba ta da shades, tace suna kare idonta daga hasken rana sannan suna kare ta daga yan sa ido. A cikin mota ya samu Al'ameen already yana jiran sa. Ya bude boot din motar aka saka wa Muhammad kayansa sannan Muhammad din ya zagaya ya shiga motar still yana kare rana da hannunsa, Al'ameen ya tsaya yana kallonsa da budadden baki "this one that you are doing as if baka saba da rana ba so kake a dauka cewa kai ba dan nan bane ba ko me?" Muhammad ya ajiye hannunsa ace "allah Ya Amen ba ka ji ranar nan ba, har cikin kwakwalwa ta nake jin ta" Muhammad al'ameen ya tayar da motar yace "welcome back to Nija" gidado yayi ajiyar zuciya yace "home sweet home" sai dai kuma a ransa bashi da tabbas din how sweet the home will really be for him. Al'ameen ya dan kalle shi yace "you look good, you look really good, har wata kiba naga kayi fa, and with that skin dole ka nuna baka san rana ba" gidado ya dan daga hannunsa yana kallon skin din sannan ya tabe baki yace "change of weather, just take me home kaji? Ka kaini inga rabin rai na ko na san na dawo Nigeria" Al'ameen yace cikin tsokana "kaga angon Safina wanna doki haka? ana ta missing amarya ko? Tunda ka bata rabin ran ka mu babu komai zamu raba the other half din" Gidado ya jefa masa wata harara yace "Safina kuma? a'a ba Safina ba Sa'adatu" Alameen yace "wacece kuma saadatu? Kar dai kace min new catch kayi" Muhammad yayi dariya sosai sannan yace "uwar safina nake nufi, sunanta Sa'adatu" Al'ameen yayi dariya shima yace "wallahi baka da kirki Muhammad, warta fa kace, yanzu sunan sirikar taka kake ambata kanka tsaye?" Muhammad ya daga kafada yace "kai ka jawo mata, why will you say she is my rabin rai?" Alameen yace "then who is your rabin rai? Am sure you are not talking about that married girl k0? Ko har yanzu bamu wuce gurin ba?" Muhammad yace "I was talking about Mama. Mama is my rabin rai please. And don't mention that girl's name. let the sleeping dog lay" Muhammad Alameen bai ja maganar ba kamar yadda gidado ya bukata, sai suka koma hirar humaira da sauran family members, daga nan kuma suka yi maganar various businesses din su da yadda suke adjusting to their responsibilities. Ana bude musu gate mama ta bude kofa ta tsaya tana kallon su har suka yi packing suka fito a tare, Gidado yana fadada murmushin sa yace "Mamana" sannan ya karasa inda take da sauri ya rungume ta, gabaki dayanta iya kirjinsa ta tsaya. Alameen ya karaso sai ta saki Muhammad tana amsa masa gaisuwar sa tare da tambayar sa lafiyar Humairah, bai amsa ba ya sunkuyar da kai yana shafa keya cikin nuna jin kunya, mama tace "Allah dai ya sauke ta lafiya, Allah ya sauke su lafiya baki daya" Alameen ya amsa a hankali sannan yayi musu sallama yace zai koma office, Mama tayi kokarin ya shigo yayi lunch amma yaki yace sauri yake yi. Suna shiga ciki Muhammad ya zauna akan kujera cikin nuna gajiya tare da fara unbuttoning shirt din jikinsa, "akwai zafi mama" mama ta karo karfin ac sannan ta zo ta zauna tana kallonsa fuskarta cike da farin cikin yanayin da ta ganshi a ciki "you look good Muhammad. I was worried ko baka samun abinci kana ci sosai" yayi murmushi "ba sosai nake cin abincin ba fa, ina ta missing abincinki, kawai dai ina samun bacci ne sosai and the weather there is good. Shine kawai. Ina abba?" tace "yana office shi da Haidar" ta kalli agogo "but they will soon be on their way". Yaran gidan suka fara hidimar ajiye masa kayan ciye ciyen da mama ta tanadar masa. Ya zuba drink a cup yana tasting sanyin sa sai yace da daya daga cikin yaran "get me ice, saurj" mama tace "kai dai kana son sanyi, ka sha ruwan sanyi ka sha kankara kayi wanka da ruwan sany" ya danyi murmushi bai ce komai ba. He sometimes feels as if his blood is too hot shi yasa yake cooling din sa down. Abu mai sanyi yana calming dinsa kuma baya saka shi ciwo. Aka ajiye bowl of ice din a gabansa tare da diba aka zuba a cikin drink din da already ya riga ya zuba a cikin cup, ya dago kansa suka hada ido da mai zuba masa ice din. Ta sha kwalliya kamar ranar ne zaa kai ta gidan miji. Jikinta sanye da doguwar riga ta shadda da ta sha aikin stones sai kyalli take yi, fuskarta with all the make up possible, daga dukkan alamu ma gidan kyalliya taje musamman aka yi mata kwalliyar aka kuma daura mata dankwalin kanta, hannayenta sun sha both bakin lalle da ja. Fuskarta dauke da murmushi. Ta miko masa kofin tare da cewa "sannu da zuwa" ya karba, amma maimakon ya sha sai ya ajiye akan table din gabansa tare da cewa "yauwa, sannunki". Ya juya gurin Mama "Mama bara inje inyi sallah tukunna" tace "gaskiya kam, kar ka ci abinci jikin ka yayi nauyi ka kasa tashi. Jiya na saka aka gyara maka dakin ka dama. Yana bude" ya wuce da sauri zuwa dakin nasa. A can ya shiga toilet ya watsa ruwa ya chanja kaya zuwa jallabiyya da wando sannan yayi sallah azahar da laasar din da yaji already an fara yi. Sai kuma ya dawo falo, mama bata nan sai safina a zaune ta dasa wa hanyar da zai fito ido, yayin mata kallo daya ya dauke kai yana jin gabansa yana faduwa, ta chanja, she looked a bit like abinda baya son ya ambata ko da kuwa a zuciyarsa ne, she cannot be. It is not possible. Amma shi ya san cewa it is very possible kawai yana so yay denying ne to protect his heart. Ya dauki wani cup din, ignoring wancan da safina ta taba, ya sake zuba ice sannan ya zuba drink a kai ya zauna yana jujjuyawa a hannunsa har sai da yayi masa sanyin da yake so sannan ya daga ya shanye ya kuma hada wani ya ajiye. Ta sauko daga kan kujerar da take kai zuwa gabansa tace "me za'a zuba maka? Akwai.... " Ya katse ta "I know menene akwai, so just shut your hole please. And please get out of my site ina son zama da family na" ta gyara zaman ta a gabansa tace "I am your family" ta shafa marar ta a hankali tace "we are your family" ya mike tsaye yana jin kamar yayi ball da kayan da suke gabansa. "goddammit" ya fada a hankali, almost inaudible dan yasan ko da wasa mama taji yana yin zagi sai ransa ya baci. A lokacin abba ya shigo, haidar yana binsa a baya da briefcase a hannunsa, duk su biyun suka saki murmushin ganin Muhammad, ya juya gurinsu shima yana kirkirar murmushi duk kuwa da yadda hankalinsa gabaki daya yake a tashe. Ya je ya rungume abba sannan kuma ya russuna ya gaishe shi, ya rungume haidar shima, haidar yana kare masa kallo yace "amma bread kake ci a can ko? Naga kamar wanda aka saka maka yeast? Mama da ta fito daga sashen ta da charbi a hannunta jikinta sanye da hijab, daga alama sallah tayi tace "tubarkallah". Abba yayi dariya shima yana jin dadin ganin dan nasa yace "zai zazzage ne ai, akwai aiki da nake ta tara masa yana nan yana jiran sa" Safina da take zaune a gefe ta gaishe da abba ya amsa mata tare da tambayar ta jikin ta, bata ce komai ba ta sunkuyar da kai tana murmushi, Haidar ya fara tsokanar ta "yau da ya dawo, tagumi ya kare. Nace wannan ciwon nata har da rashin yaya" ta dan harare shi cikin wasa amma bata ce komai ba sai mama tace "kinyi sallah kuwa safina? Dan miji ya dawo kuma sai ki zauna ki saka shi a gaba kina kallo ba zaki je kiyi sallah ba?" safina ta mike da sauri ta shiga wani daki da yake cikin falon. Suna zama sai ga mufida ta shigo gidan da gudunta, tazo ta rungume Muhammad tana dariya, ya daga ta daga jikinsa hana murmushi, yana kin dadi a zuciyarsa "yar autar Mama, ke da nace miki zan zo har gida ina same ki?" Ta bata rai "da zaka tafi ma cewa kayi zaka je muyi sallama kuma ba ka je ba. Shi yasa naki jiran ka yanzu" yace "ayi hakuri, nayi niyyar zuwa wallahi sai abubuwa suka duke min hankali, sai da na shiga jirgi na tuna" tace "zanyi hakurin but I need one more squeeze" ta fada tana kara rungume shi. Bayan Mufida ta gaishe da kowa sai suka hadu gabaki daya suka tafi dining suka fara zuba abinci, tun kafin su fara ci sai ga Safina ta dawo, fuskarta tana nan da kwalliyar ta, tana shiga gurin Mufida tace "hey in law! I was about to ask about you sai na manta" Safina tace "nayi fushi ai. Tunda kinga yayanki ai dole ki manta da ni'" Mama ta juyo tana kallon Safina tace "Safina wannan fuskar kuwa kin wanke ta? Ta yaya kika yi alwala da wannan kwalliyar?" Safina ta dan yi murmushi nervously "Mama nayi, ai ba zata fita ba dama" Mama ta girgiza kai "ai kuwa dai in bata fita ba alwala ba tayi ba. Ki koma ki wanke ta tas ki sake alwala ki sake Sallah. Ai ya ga kwalliyar taki" Safina ta dan bata rai "Mama nayi alwala kafin inje kwalliyar fa" Mama tace "tun safe kenan? Alwala tun safe har la'asar ai ya kamata a hakura da ita ko?" Safina ta juya ta koma ciki, Mama ta gyara zaman ta tana cigaba da zuba wa Abba abinci. Haidar yayi dariya, Mufida tace "Mama kin ba da Safina a gaban Haidar, a gaban kuma mijinta" Mama tace"ga Abban ku nan a zaune shima ai. Dole mu gyara mata mata tarbiyyar ta ai, ko mijin nata ne yayi ba dai dai ba dole a gyara masa ballantana ita, she will soon become a mother, idan babu tarbiyya ai mun shiga uku baki daya". Muhammad ya kware da abincin da yake ci. Abba ya zuba masa ruwa ya mika masa, ya karba ya sha amma still yaji abincin ya tsaya masa a makogwaronsa ya ki wucewa, wani zafi yaji jikinsa ya dauka. Ya fara panning fuskarsa da hannayensa sai ya lura kowa na gurin shi yake kallo. Abba yace "lafiyar ka kuwa?" Muhammad ya sake daukan cokalin ya debi abincin yace "lafiya lau. I am not feeling good ne kawaj" Mama tace "kace lafiya lau kuma kace you are not feeling good, Wanne ne kenan? Kar fa mu je ko heat stroke zaka samu dan tun dazu kake complain din zafi" Haidar ya mike tare da kara karfin ac sannan shima ya tambaye shi "are you okay Yaya?" Muhammad ya kirkiri murmushi tare da gyada kai, yana jin babu dadin yadda duk suka shiga damuwa lokaci daya saboda shi. "It is okay. I am okay yanzu" ya fada yana sake kai lomar abinci bakinsa duk da waccan lomar har lokacin bata wuce ba. A zuciyarsa ya san abinda duk wadannan maganganun suke nufi amma ya kasa barin kwakwalwarsa ta yarda. Mama tace "'in ka cigaba da jin zafin dai kayi magana aje asibiti, tun kafin abun ya zama babba" ya gyada kai kawai tare da kokarin cigaba da cin abincin da yake gabansa. Sunanan zaune Safina ta sake dawowa, ta wanke fuskar tas yanzu, daurin dankwalin ma daga dukkan alama an kwance shi an sake, Mama tace "yauwa, ko ke fa, yanzu har kinfi kyau ma" ta danyi murmushi tana sunkuyar da kanta kasa, Mama ta nuna mata kujerar kusa da Mufida daga right dinta tace "zauna to ke ma kici abinci, tun safe banga kinci komai ba kina ta kwalliya" sai ta zagaya ta zauna a left din Mufida, kujerar da take kusa da Muhammad. Ta zuba abinci ta fara ci, yana jin idanunta a kansa amma bai ko kalli inda take ba, he tried as much as he can to not ruin the moment for his family. Suka yi ta hirar su suna bashi labarin gida yana basu labarin can. Bayan sun gama kuma sai suka sake dawowa falo ya zauna yana ta yiwa Abba bayanin tarukan da yayi attending da matsayar da aka samu a tarukan and what they mean to their business. Suna nan tare har magrib, suka je suka yi sallar suka sake dawowa suka cigaba da hirar su, zuwa lokacin Muhammad ya dan ware, trying not to look at side din da Safina take zaune duk kuwa da cewa yana jin yadda ta zuba masa ido a jikin sa. Daga baya sai ga mijin Mufida yazo daukan ta, shima ya shigo yayi joining hirar ta su, sai kuma suka yi dinner tare sannan Abba yace kowa ya zo ya tafi gidan sa. Mufida ta fara tsokanar Safina "Safina ki kara wa Mama ko sati biyu ne mana" Mama tace "ina fa, ta tafi gidan mijinta ya cigaba da jinyar a can. Tun dazu dama na saka an kai yan aikinta gidan dan su gyara musu kafin su tafi" Babu kunya sai ga Safina ta jawo akwatin kaya ta fita da su waje, tana ganin Muhammad ya tashi kuwa tayi wa Mama sallama, dama Abba ya riga ya shiga ciki, ya fita ta riga Muhammad din shiga motar ta zauna, maybe tana tsoron kar yayi mata irin na ranar nan. Ya tsaya yana kallon ta kawai a ransa yana tunanin da ace daya motar tana nan da ita zai je ya shiga yayi tafiyar sa ya barta anan ya ga yadda zata yi. Amma kuma Mama tana tsaye a bakin kofa tana kallon su, yayi sallama da su Mufida ya zo ya shiga motar yana bata wuta Mama ta leko tace "ka tafi a hankali fa, ban da gudu, kai a guje dama kake driving dinka sai kace dan tsere" yayi murmushi "to Mama, ba zanyi gudu ba" tace "Allah ya sa" ya ja motar a hankali suka fita daga gidan, amma ana rute gate ya fige ta a guje saura kadan Safina ta hantsula, tayi sauri ta gyara zamanta tare da saka seat belt. Suka fara tafiya da farko in silent, Allah Allah yake yi suje gida ba tare da tayi magana ba ballantana tayi confirming abinda yake suspecting. Har ya fara murnar ba zata yi ba sai kuma tayi din "ya hanya?" Yayi kamar bai ji ta ba ya kara gudun motar sa, sai kuma tace "you run away, gashi kuma ka dawo" ya dan daga kafarsa ya juyo yana kallon ta yace "excuse me? Me kika ce?" Ta maimaita "cewa nayi ka gudu, gashi kuma ka dawo" yace "ban gane na gudu ba? Gudun me zanyi? Run away from what?" Tace "you run away from me" yace "and why will I do that?" Tace "because you found out that you cannot resist me. Shi yasa ka gudu" Sai da ya danyi karamar dariya "you are delusional. You and I know that that thing that you think happened…….." Ta katse shi "that I think happened? Kana nufin bai faru kenan ba. Kana nufin I imagined it? Okay wanne bangaren nay imagining the first round or the second" yaji kamar yaje ya jefa su a rami gabakidaya su mutu kowa ya huta. Yana girgiza kansa cikin dacin rai yace "I wanted to not talk about it now, amma tunda kin kawo topic din let me spell it out for you. Na farko I did not run away from you or from anything, na riga nayi planning tafiya ta before that thing you think is something happened. So idan kina tunanin it means something to me ki daina, it means nothing, you mean nothing and will never be anything to me. Abu na biyu kuma mafi muhimmanci shine ni da ke gabakidaya mun san cewa what happened that day wasn't natural, you did something to me, I don't know what amma ke kin sani kuma you are going to tell me one way or another. Me kika yi min?" Ya fada almost shouting. Tayi kokarin matsawa daga kusa da shi yadda ransa ya baci gani take kamar zai kai mata duka. "'Ba zaki fada ba?" Ya sake yi mata tsawa. Ta rufe fuskarta da hannayenta da suka sha lalle tace "ni banyi maka komai ba. Ni babu abinda nayi maka". Yayi horn a bakin gate mai gadi ya bude masa kofa ya shiga da motar yaje yayi packing ya juyo yana kallon ta "Ke munafuka ce Safina. Baki da gaskiya ko kadan. Kin aikata abinda kika aikata and you have the guts to spill out trash from that hole in your face kina gaya min maganar banza? You did something to me ke ma kin sani, you thought idan naje gadon ki I will fall in love with you ko? Haka kike tunani? To abinda baki sani ba shine what you did made me hate you the more, made me despise you the more, your gutter behavior and your trash of a body disgust me. I am going to find out what you did and I am going to use it as a pass to my freedom from you". Ya bude motar ya fita sannan ya buga kofar motar da karfi. Part din sa ya wuce, sai daya bude ya shiga sannan ya tuna bai fito da kayansa daga mota ba, ya juya ya fita ya tarar har lokacin tana zaune a mota tana kuka. Ya fito da kayansa ya ajiye ya bar mata nata a ciki. Mai gadi yazo da sauri ya gaishe shi ya dauki kayan ya wuce ciki. Sai a lokacin ta fito daga motar, ta tsaya tana kallon sa suna magana da mai gadin, yan aikin ta biyu da cousin dinta da suke gidan suka fito ta bude booth ta basu kayan ta suka shiga da shi cikin gida. Sai da ya gama yiwa mai gadi magana ya juya zai tafi sannan ta kira sunansa "Muhammad" ya dakata amma bai juyo ba. Ta karasa bayan sa ta tsaya sannan tace "I am pregnant" still bai motsa ba ballantana ya juyo ya kalle ta. Ta cigaba "I wanted to tell you tun kana can, amma ba ka daukan waya ta ba ka duba messages dina. At least idan banci albarkacin soyayyar da nake yi maka ba ai ya kamata yanzu in ci albarkacin abinda yake ciki na" Ya yi gaba, pretending kamar bai ji abinda ta fada ba amma ransa tafasa yake yi. Yana zuwa dakinsa ya zauna akan gado ya dafe kansa da hannayensa guda biyu. "Ya Salam" ya ambata. Yanzu shi ya zai yi da wannan yarinyar ne? Ta zame masa karfen kafa, Tashin hankalin sa guda uku ne akan wannan cikin. Na farko ya san yanzu ¡yayen sa sun sani, za kuma su dauki hakan a matsayin ya karbi auren kenan. Hakan kuma zai kara masu wahalar amincewa idan yace zai rabu da ita. Na biyu kuma he just can't imagine Safiyya seeing Safina pregnant with his child, tunda dai tasan yadda aka yi aka samu cikin, it will break her to pieces. Yasan cewa Safiyya ma zuwa yanzu akwai tabbacin tayi irin wanna mu'amalar da mijinta Mukhtar, amma ai shi bashi da alaka da Mukhtar but Safina is like a sister to her. Abu na uku kuma mafi muhimmanci shine ya zai yi da yaron ko yarinyar da zata haifa masa? Anya zai iya son su yadda ya kamata kuwa? Considering irin tsanar da yayi wa mahaifiyar su. Baya son ya zama bad father kamar yadda yake bad husband. Her🧕🏻 Kamar yadda nace na gama shafe babin Mukhtar haka nayi, ban kuma ko da tayar da maganar ba. Sau da yawa Mommy ta kan saka ni a gaba tana so muyi maganar and she will be like "yaron nan ya dage dai shi ba zai yi sakin nan ba. Ai kuwa ¡yayen ne ya kamata su matsa masa. Maybe ya dauka bluffing kike yi ba da gaske kike ba maganar court din nan. To in bai sake ki bama in aka rufe shi dole alkali ya raba auren kinga a yayi biyu babu" in tana yin maganar na kan chanja topic ko kuma in ina da abinyi inyi excusing kai na in tafi inyi. Twins sun zo da weekends sun gan mu and I guess Mommy ta gaya musu abinda yake faruwa, suka zo suka saka ni a gaba "yanzu Yaya Fiyya ya ma za'a yi ki barshi? Ai wallahi ki kai shi kara. Make him pay for what he did. Shege mugu azzalumi" sai nayi murmushi kawai na rabu da su. Daga baya suka ce sai sunje har gida sun same shi, anan ne nayi magana na hana su nace babu ruwan su a ciki, maganar manya ce kuma manyan will take care of it. Har lokacin Mukhtar bai hakura da turo min messages ba, na safe daban na rana da ban na dare da ban. And a cikin su all maganar sa daya ce "ina matukar son ki Safiyya, dan Allah ki bani dama in gyara kurakurai na. I want to take care of you and our son" Or something like that. Ranar nan kuma har da cewa "duk abinda ya faru laifin ki ne. Da kin karbi soyayya ta tun farko da duk haka bata faru ba. We will have been happily married by now. Wallahi Safiyya ina son ki" A lokacin ne na bashi amsa "ta waya zaka turo divorce note din ko kuma a takarda zaka rubuto? In a waya ne please send it to my email for safe keeping". To take my mind off things sai na mayar da hankali kan renovating Oasis, a bawa wani kamfani contract din gyaran buildings din ciki har mun zauna mun gama tsara komai. Na kuma samu landscape designer shima mun tsara yadda design din harabar gurin zai kasance. Duk sun fara aiyukan su already. Sai na mayar da gurin wajen zuwa na in debe kewa, wani lokacin mu tafi tare da Daddy wani lokacin har da Mommy da Mustapha. Sai na fahimci cewa Daddy yana jin dadin zaman Abuja yanzu dan ko maganar komawa Kano baya yi. Ya kan i min maganar Mukhtar shima sometimes, yace lokaci ya bawa Uncle Ahmad ya ga idan zai iya controlling dansa, if not duk abinda muka yi ba zamu zama mu muka tozarta familyn ba, cos munyi duk abinda zamu iya yi. Ranar nan na tafi Oasis ni kadai, Daddy yayi baki wani abokinsa da matarsa dan haka shi da Mommy suna gida, and I noticed motar Mukhtar tana bina a baya through my center mirror, Ban kula shi ba na cigaba da tafiya ta har naje Oasis din and I told ma'aikatan da suke aiki a gidan cewa someone has been following me, kar su barshi ya shigo ina zargin mugu ne. Ai kuwa ina jin su suna hayaniya a bakin gate, har yan unguwa suka fara taruwa and I guess he ran away. A lokacin ne na kira barrister Umar and told him ina bukatar body guards, like always, he showed concern amma nace masa zamuyi maganar later. Bana son in saka su a cikin maganar har sai Mukhtar ya zabi one of the options din da na bashi. Babu bata lokaci ya samo min guards din manyan gaske su uku, and they also have military training, nan take na dauke su aiki, aikin su shine kula da lafiya ta. Duk inda na je suna bina a baya. Ba wai a mota daya muke tafiya ba but suna motar su suna bina a baya ba tare da ya zama obvious cewa suna bina ba. A gida ma kuma they keep guard, sun kara zama another layer of security a gidan. Na nuna musu pictures din Mukhtar da na motar sa and I asked them to keep a look out for him, bana sonsa anywhere close to me, Ai kuwa ranar nan na sake fita ni kadai purposefully dan ina son ya bini din, like I expected, he followed me har Oasis, na shiga nay packing and my guards packed after me na gaya musu "in yazo ku kama shi ku mika wa police shi, in yayi resisting ku dake shi" Ai kam yaci duka, dan dama na san zai vi resisting din, sai da suka yi masa laga laga sannan suka mika shi hannun yan sanda da sunan yana stalking dina, I thought zai gaya musu ni matar sa ce but he didn't, maybe he is not as dumb as I thought. Sam ban gaya wa Daddy ba sai da uncle Ahmad ya kira shi ya gaya masa wai Mukhtar yana hannun police, shima kuma yace ba zaiyi bail din sa ba. A haka dai sai da yayi three days sannan wani kanin umman sa yaje yin bail din sa, a nan barrister Umar yaje on my behalf kuma ya nemi a tura su court dan yana son Mukhtar yay signing restraining order against me. They went and he signed. A lokacin na kara fahimtar cika baki yake yi ashe da kurin banza. I continued waiting for my divorce paper and it finally came. Ranar ina daki a zaune na gama interviewing wan digital designer da nake son dauka aiki dan yake zana mana patterns masu kyau na atampopi da laces, sai ga Mommy ta shigo da takarda a hannun ta. Ta zauna tana kallona fuskarta da murmushi sai kuma ta miko min tace "finally ya rubuta" na karba ina jujjuya takardar a hannuna duk kuwa da cewa a zuciya ta na san ta mecece. Tace "Ahmad ne da kansa yazo ya kawo wa Daddyn ki, yace sai da suka saka shi a gaba shi da mahaifiyarsa suka ce zasu tsine masa sannan ya rubuta. He kept hoping cewa zaki chanja mind dinki ki koma gidan sa" nayi shiru dai ban ce komai ba. Sai kuma na mayar mata da takardar "ku zaku rike a hannun ku ai" tace "ki fara budewa ki karanta. Saki baya tabbata sai sakon ya isa zuwa ga wadda aka saka". Na bude na karanta "Ni Mukhtar Ahmad Muhammad, na saki matata Safiyya Adam Muhammad saki daya. Ina fata da kuma saka ran watarana zata fahimci girman soyayyar da nake yi mata za kuma ta yafe min mu dawo mu cigaba da auren mu" Na ninke ta na mika mata. Ban damu da adadin sakin da yayi ba in dai yayi din shikenan, abinda na sani shine ko duniya zata taru a kaina ba zan koma wa auren sa ba. Mommy ta karba ta mayar cikin envelope din ta tace "to alhamdulillah, Allah ya sa haka shi yafi alkhairi. Insha Allah ma hakan shine mafi alkhairi" na sunkuyar da kaina kasa nace "Amen" ta mike tsaye tace "sai ki fara lissafin idda kuma" na girgiza kaina nace "babu iddar sa a kaina" sai ta fadada murmushin ta "masha Allah. To magana ta kare kenan. Bara inje in sanar wa da Adam. Allah ya kawo miki na gari wanda mutuwa ce kadai zata raba ku" nace "Amen" a hankali, sai kuma nabi bayanta da kallo ina tunanin har yanzu bata hakura da hada aurena da Mustapha ba. A gurin ta wannan rabuwar da muka yi da Mukhtar kamar second chance ne ta samu na hada ni da Mustapha. Sai da ta fita sannan na sauke wata katuwar ajiyar zuciya. Free at least. Naji kamar an dauke min wani katon dutse daga kaina. Na rufe idona tare da saka hannayena biyu na rufe fuskata da su "'alhamdulillah, alhamdulillah,alhamdulillah" Na jima a haka sannan na bude fuskata na dauko waya ta na kira barrister Umar "hello barrister, Ina bukatar gain ka Please, yaushe kake free?" And then two days later muka hada case file akan abinda ya faru da ni. Hankalin barrister Umar ya tashi sosai da na gaya masa abinda ya faru da ji. Babu yadda bai yi da ni ba akan in barsu suyi bincike amma nace su ajiye file din kawai, he even bluntly told me cewa Mukhtar yake zargi. "That guy da yake binki ranar nan" na girgiza kaina "just keep the file in your firm. Let's wait and see. Duk ranar da ya ambaci da na a matsayin dansa a ranar zaku kai shi court ko bani da rai, and make sure he gets the highest possible sentence". A haka na bar case din a hannunsu, legal firm ne suke da shi dan haka ba wai barrister Umar ne kadai ba, ko babu shi akwai wasu, and the case is with them. And that was another weight off my shoulders. Ina komawa gida na hadu da Mustapha. Ya bini cikin gida yana min magana. Muka tsaya a gaban stairs. Yace "Mommy ta gaya min what happened. Allah ya sa haka shine mafi alkhairi" nace "Ameen, Nagode" yace "are you now done with him? Zan iya cin ubansa yanzu?" Nayi murmushi "be careful, am sure he is angry yanzu, kar kaje garin fansa a fanso ka" yayi murmushi "you don't know me, you have no idea what I can do. Will you like to know" na girgiza kaina "no thank you. But just know that na gaya maka abinda Mukhtar yay because I think you deserve to know. Duk abinda zai faru a tsakanin ku babu hannuna a ciki. Ko me zaka yi masa bani na saka ka ba kuma ba dan ni kayi ba. Is that clear?" Yace "yes ma, sound and clear" na wuce shi na fara hawa stairs and I saw Mommy looking down at us, sai kuma ta juya kamar ba kallon mu take yi ba ta koma ciki. Two Days after that ina daki a zaune ta shigo. "Safiyya shirya mana muje mu duba Safina. Bana jin dadin yadda alakar ku take tafiya wallahi. So nake yau muje mu wuni a gidan ta" na fara girgiza kaina "Mommy bana jin dadi" na dafe kaina "kaina ne yake ciwo" ta saki baki tana kallona "yanzu fa na ganki kuna ta hira da Esther a kasa, and suddenly ciwon kai yazo dan nace muje gidan Safina?" Na zauna tare da dafe kaina "yanzu bayan na hau naji kaina ya fara ciwo" tayi ajjiyar zuciya "ai shikenan, Allah ya sawake" Tana fita na koma na kwanta ina daddanna waya ta. I have been thinking about him a lot, duk da ma dai ina kokarin keeping kaina busy to stop myself from thinking about him. Dan future din mu together is very blurry ba kuma na son sake saka mu a cikin heartbreak irin wanda muka shiga a baya, ko kuma ma more than that. Na dan jima a haka ina scrolling blindly through social media, ba na ma gane me nake karantawa sai kuma a mike na ajiye wayar na shiga toilet nayi wanka na fito and I took my time to dress up elegantly. Very classy but less flashy. Na saka turare na yafa mayafì na sannan na dauki glasses dina na saka. I looked at myself in the mirror and smiled. Na san ba lallai bane mu hadu da shi a gidan ba, but at least zuwan nawa da kuma yadda nake looking plus the fact that I am now single zai hana Safina bacci a daren yau. Wannan shine target dina. But what if muka hadu? Na tambayi kaina tare da rike kirjina saitin zuciya ta. Naji kamar in fasa zuwa but wani abu da nake ta tura wa kasan zuciya ta for months shine yake taso min. My heart hoped with every vein and artery in it that my eyes will see him. Na bude kofa na fita baranda a dai dai lokacin da Mommy ita ma ta fito daga dakin ta. Ta tsaya tana kallona da baki a sake, I smiled at her nace "na shirya Mommy" ta rufe bakin tace "ciwon kan ya warke kenan?" Na sake murmushi sai na wuce ta na sauka kasa. Ina jinta ta sauko tana kiran Mustapha, na wuce falo na tafi gurin Daddy. Ina shiga na cire glasses dina na rike su a hannu na. Yana zaune yana kallon news, na gaishe shi and naga alamar yaji dadin ganina. "you look great" yace nayi murmushi "Thank you Daddy" sai kuma na gaya masa inda zamu je and ask him if he needs anything kafin mu tafi, duk da dai twins suna gidan kuma ba da su zamu tafi ba. And akwai yaron da yake masa errands a part dinsa. Ya girgiza kai yace "bana bukatar komai. A dawo lafiya" na mike na mayar da glasses dina sannan na fita. Motar Mustapha naga an fito da ita, na tsaya a gefe ina jiran su fito, Mommy ce ta fara fitowa tana ta lissafa wa Esther abubuwan da zata yi kafin mu dawo. Tana zuwa ta shige bayan motar, na gane abinda ta shirya, tana so mu zauna tare da Mustapha a gaba and I didn't care, Esther ta tsaya tana kallona tace "kinyi kyau Madam" nayi mata murmushi tare da thumbs up sannan na wuce na shiga gidan gaba, Mustapha ya fito shima da sauri ya shiga. Muna daukar hanya Mommy ta fara fada "yaron nan mijin Safina she ya dawo? Amma ko a ransa bai yi tunanin ya kamata yazo ya gaishe mu ya duba jikin Daddy ba. Wannan wanne irin siriki ne Allah ya hada ni da shi? Ko waya bai yi ya gaishe mu ya gaya mana cewa ya dawo ba. Ita kuma munafuka tayi shiru dan bata son fadar laifin sa dan kar inyi fada..." na jawo ear piece daga cikin jaka ta na saka a kunne na sannan na kunna kida a waya ta. Ina kallon Mustapha yana kallo a tare da murmushi amma bai ce komai ba. Muna yin packing a gidan I saw his car, I saw his two cars, jikina kuma ya bani yana gidan. Na bude kofa na fita for the first time ina karewa harabar gidan kallo, naga motar Mommy a gefe wadda ta bawa Safina. Ni kaina bani da tabbas din abinda nake aikatawa but zuciya ta tana ta zuga ni. Na san a cikin biyu za'a yi daya, ko dai in breaking heart din Safina ko kuma ni in kwaso nawa heartbreak din. Zuciya ta kuma yanzu bana jin tana da karfin karbar another heartbreak, Nabi bayan Mommy zuwa part din Safina, ina shiga naji nadamar zuwa ta sauko min, wani feeling nake ji na kishi a cikin zuciyarta. Kishi mai zafi but na daure. Na samu guri na zauna tare da daukan kafa daya na dora akan daya. Mustapha ya zauna opposite me tare da kwalla wa Safina kira "kina ina ne wai?" Naji ta amsa daga ciki. Mommy ta shigo tana mita. "Yana gidan, Zan ga karyar rashin kunyar sa yau. Zan gani idan ba zai fito ya zo ya gaishe ni ba" na gyara zama na. This is a drama worth watching. Ni na san rikicin Muhammad. Idan ya rikice tsohuwar mota ma ta fishi dadin sha'ani. Ba'a controlling dinsa. Ina nan zaune aka kawo mana drinks aka ajiye, Mommy ta mayar da mitar ta kan Safina "ba zata fito bane ba ko me? Lemo muka z0 sha ne wai? Idan dangin mijin sunzo suma haka kike musu?" Safina ta sake amsawa daga ciki sai gata ta fito tana daura dankwalin. And she startled when she see me sitting there looking all pretty and elegant, one leg on top of the other. Sai da Mommy tayi mata magana "Safiyya ce kike kallo haka? Ko don ki ya samu matsala ne?" Ta wuce ta gaba na, jikin ta yayi matukar sanyi taje gurin Mommy "Mommy sannu da zuwa, Ban dauka tare zaku zo ba shi yasa" Mommy ta tabe baki "kin santa kamar mai aljanu, da tace ba zata zo ba kuma sai ta chanja shawara" ina jin su ta gaishe da Mustapha sannan ta juyo tana yi min magana, nayi pretending kamar banji ba sai Mustapha ya dan buga kujerar da nake kai, na kalle shi sai ya nuna min Safina, na cire ear piece din da yake kunnena ya yi mata murmushi brightly nace "hi Safina. Ya kike? Ya mijin ki? Hope yana gida dai yau mu gaisa" And she lost all colors, her white skin became very pale. Mommy ta dora daga inda na tsaya "nima ina fatan yana gidan. Dan yau sai na yi masa wankin babban bargo a gidan nan......" Na mayar da ear piece dina cikin kunne na na cigaba da jin waka ta. Sai dai har cikin bakina daci nake ji. Wani iri nake ji a raina. Wani irin kishi nake ji a zuciya ta. Kishin da na jima ina dannewa ranar sai naji yana kokarin yafi karfina. Mommy ta tura Safina ta kirawo mata Muhammad. Bata jima ba ta dawo "Mommy bacci yake yi" "bacci kuma?" Mommy ta fada "wanne irin bacci? Kuma ni ina kiransa ba zaki iva tashi sa ba?" Safina tayi kamar zata yi kuka, Mommy ta saka salati "wai tsaronsa kike ji ne ko menene?" Safina ta zauna akan hannun kujera "Mommy ai ba yanzu zaku tafi ba. Kafin ku tafi zai tashi" amma kamar kara zuga Mommy tayi, haka ta juya ta dake komawa sai gata ta sake dawowa. "Kofar dakin nasa ma a rufe take" Mommy tace "wanne irin kofa a rufe? A cikin gidan sa in zaiyi barci sai ya rufe kofa? Wanne irin aure kuke yi ne wai?" Safina bata ce komai ba sai Mommy ta sake cewa "kinga yadda kika kara lalacewa kuwa? Da da baya nan kinyi kiba kinyi kyau amma daga dawowar sa j yadda kika koma. Gaskiya ba zan iya cigaba da yin shiru a lamarin nan naku ba" ta dauko wayarta, Safina tace "Mommy wa zaki kira?" Mommy tace "'uwarsa zan kira, ita ta kira shi tace yazo nan ya same ni ina neman sa tunda ke ba zaki iya zuwa ba" Safina ta mike tsaye, obviously distressed. Sai ta wuce mu tayi hanyar kitchen, sai kuma ta leko ta kira sunana "Safiyya dan zo mana ki ga girkin nan, ke ce gwanar girki" ina jinta amma yanzu ma sai da Mustapha ya sake taba kujera ta sannan na cire abin kunne na. Mommy ce tace min "je ki ga wacce kwamacalar take hada mana a kitchen din". Ni nasan babu wani girki da zata nuna min, but bani da uzurin kin zuwa, na tashi na tafi yayin da Mommy ta fara waya da mama Muhammad. Ina shiga kitchen din ta ja hannuna "I want you to leave this house right now" na gyara tsayuwa ta nace "or what? Me zai faru idan ban fita ba?" Tace "zan gaya masa. I swear to God idan baki rabu da shi ba zan gaya masa" nayi tsaki "wa ya rike ki? Je ki fada masa mana. Matar da ko bedroom din mijinta bata da ikon shiga ita take cika wa mutane baki. Please go and tell him and I assure you zaki farka ne ki ganki a gadon asibit'" and the look on her face was almost pitiful, but I didn't pity her, na je gabanta na tsaya nace "he is mine. You stole him. I am taking him back. Na gaya miki tun dadewa, da kafafuwan ki zaki ruga a guje ki barshi kamar yadda kika kawo kanki da kafafuwan ki". Ta danyi murmushi tace "haka ne. Ni na kawo kaina. And I know he will choose you over me. But do you think he will choose you over his child" ta fada tare da kama hannuna ta dora akan marar ta. Nayi sauri na janye hannu na ina jin gabaki daya jinin jiki na yana kafewa, She is pregnant, Na gaya wa zuciya ta. She is pregnant with babyn Muhammad. Naji jiri yana kokarin dibana. Ta kara matsowa kusa da ni tace "he is mine. Nawa ni kadai. And I will do anything to keep him".Sai kuma ta juya da sauri ta fita daga kitchen din. Sai da na dafa bango sannan na iya tsayawa sosai. Wani daci nake ji a cikin zuciyata. No matter how I tried babu abinda nake gani a ido ma sai Muhammad da Safina doing the deed. Har wani baci nake ji a cikin zuciyata. Na lallaba na fito bakin kofar kitchen din ina kallon Mommy suna magana da Mustapha amma bana jin abinda suke cewa dan ji nayi kunne na ya toshe gabaki daya. Na cigaba da bin bango ina tafiya har nazo tsakiyar falon a dai dai lokacin da Muhammad ya turo kofa ya shigo. Yana shigowa idonsa ya sauka a kaina. He looked startled kamar zai juya ya koma a guje sai kuma yayi regaining kansa ya tsaya yana kallona. Jallabiyya ce a jikin sa ruwan toka mai duhu da ta dace sosai da fatar jikin sa, sumar kansa da ruwa a jiki daga alamar daga wanka ya fito dan har akwai alamun ruwan a jikin jallabiyyar ta sa, idanunsa da fuskarsa suna nuna alamar yayi bacci mai nauyi. Sai naga kamar bai taba yi min kyau irin yau ba. Kamar ba'a taba yin namiji mai kyawun sa ba. It took him a lot of efforts to take his eyes off me ya mayar da su kan Mommy sannan ya durkusa a gaban ta yana gaishe ta. Bata amsa ba ta kama wanke shi din kamar yadda tayi niyya "wato da baka yi niyyar fitowa ba sai da na kira Zainab ko? Ita ce kadai zata yi maka magana kaji ni ban isa in aika a kira ka kazo ba ko?" Ya sake dago kai ya kalle ni sannan yace "ina bacci ne, ban san kunzo ba, sai yanzu ta kira ni tace kun zo" tace "na tura matar ka ai tace dakin a rufe. Wanne irin aure ne wannan. Ni fa ban ganewa auren ku ba sam. In ba zaka yi ba babu lallai babu dole ka dawo min da yata ina son kaya ta. Ga Safiyya nan ma da auren ta ya mutu babu abinda ya same ta, ita ma......." "Safiyya?" Ya maimaita tare da sauri ya dago kai ya kalle ni. Ina cikin idonsa na karanto abubuwa da yawa. Naji wani karfi ya zo min na zagaya na dauki jakata na mayar da glasses dina sannan cikin sauri na ratsa tsakiyar falon nayi hanyar waje, Mommy ta katse maganar da take yi tace "ina zaki je" ba tare da na tsaya ba nace "gida zanje, kaina ne yake ciwo" ina wuce shi ya mike tsaye "Piya!" Ya kira sunan da na manta rabon da inji an kira ni da shi. Sunan da ya kara stirring abubuwa da yawa a cikin zuciya ta. Amma kuma ido na babu abinda yake gani sai shi da Safina, making a baby. Na wuce shi ba tare da na kalle shi ba, Safina ta mike tsaye da sauri a lokacin da shima ya biyo baya na da sauri "Piya" ya sake kira na amma ban waigo ba sai ma saurin dana kara nayi hanyar gate. A cikin falon muna fita Safina ta juya gurin Mommy tace "congratulations. You just ruined my life. Me yasa ba zaki yi shiru ba?" Sai ta juya da sauri tayi akin ta. Mommy ta bi hanyar da muka fita ni da Muhammad da kallo sannan ta bi hanyar da Safina ta bi ita ma da kallo sai kuma ta bude hannun ta alamar tambaya "me ya faru wai? me nace?" Ya juya tana kallon Mustapha ta sake cewa "me nace?" Mustapha ya daga kafada alamar shima bai sani ba. Maman Maama✍🏻 Longest episode ever ko?😁 I just want to finish this novel but I am loving it [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Forty Nine : Broken *Contact Bojuwa HERBAL'S for all your* *kayan mata for* *Amarya* *Uwargida* *Bazawara* *Mai jego* *Saiwowin sanyi gangariya da na dahuwar kazar sababi har da na tattabaru da ciccibi all from Chad.* *Kayan gyara masu kyau da inganci kala daban daban, special maganin sanyi for women of class*. *Contact Surayya HALIN YAU on* *08032773332* *. . . Ina zuwa gate na kama kokawa da kofar na ma rasa inda zan murda in bude, il nake yi kamar wuta ce take ci a cikin zuciyata, Mai gadin su ya taso da sauri ya bude min amma kafin in fita Muhammad ya karaso. Kusan tare muka fita nayi kokarin kara sauri amma sai ya rike jaka ta, na juyo a fusace na nuna shi. "Sakar min jaka" naga yanay in sa gabaki daya ya chanja fuskar sa tana nuna alamomin tambaya da yawa "Safiyya? Me ya bata miki rai haka?" Na sakar mass jakar nayi gaba, dan rainin hankali, wato ni zai raina wa hankali har yayi min wata tambaya marar ma'ana. Ya sha gabana da sauri yana kokarin hada ido dani, saura kadan muyi karo saboda saurin da nake yi. "Piya dan Allah ki tsaya muyi magana" na zagaye shi naci gaba da tafiya, bana son ganin shi sam, bana kuma son jin muryarshi dan ji nake yi kamar in shaki wuyansa, munafiki. Ya sake rike mayafi na, "Piya Please now. Me nayi ne wai ni?" Na juyo da sauri ina kallon sa cike da masifa sai na nuna masa gidan sa nace "she is pregnant" nan take naga yanayin fuskar sa ya juye zuwa guilt, pure guilt. Ya saki mayafin nawa a hankali, bana bukatar wani dogon bayani kuma na san ba karya take yi ba, gaskiya ta tada this time around. Naji abinda ya tokare min a kirji ya fadje6, wata kila ma tare da zuciyar tawa suka fashe. Kawai sai wani kuka yazo min, ai kuwa na fashe da kuka. Yayi sauri ya kara matsowa kusa da ni "Piya!" Kuma sai ya kasa cewa komai, yayi attempting magana ya kai sau biyar amma ya kasa furtawa. Na juya na barshi anan a tsaye na cigaba da tafiya ta ina kuma cigaba da kuka na. Idan ka ganni zaka dauka sakon mutuwa aka aiko min ko kuma patient ce ni a psychiatry. Ya cigaba da bina, "Please Safiyya people are looking, ki daina wannan kukan, let me get my car and take you home. We will talk on the way" ba tare da ma juyo ba nace "I don't care about people, I don't care about anything, I don't care about you or your wife or your baby. Ka juya ka koma gurinta and don't ever talk to me again. Karma ka kara nuna ka san ni. I wish ban sanka ba a rayuwata" Ya sake zagayowa gaba na, ya tare min hanya, kokari kawai yake sai na kalle idonsa ni kuma naki daga kai in kalle "look at me Safiyya, Let me get the car. We will talk" na karbi jakata daga hannun sa sannan na dake shi da ita a kirjinsa, "Get out of my way, get out of my site, Get out of my life, Me zaka ce min? Zaka ce min ba naka bane ba?" Yayi shiru bai ce komai ba amma tsananin tashin hankali ya bayyana a fuskar sa. Na nuna shi da yatsa na "babu ni babu kai har abada" na sake zagaye shi zan cigaba da tafiya sai va sake rike jaka. "Piya....... Dan Allah..... Ki tsaya muyi magana" na sake sakar masa jakar sai kuma kawai na durkusa a inda nake dan ji nayi ba zan iya cigaba da tafiya ba. Na kife kaina akan guiwowina na cigaba da russ kuka kamar wadda aka ce Daddy ya mutu. Ina jin wasu mutane suka zo wucewa suka yi masa magana ya basu amsa amma banji abinda suka ce ba sai suka wuce. Sai naji motsinsa shima ya zauna a kasa a kusa da ni, ina iya jin kamshin sabulun da yayi wanka dashi. Ji nake yi a raina tamkar komai na rayuwata ya tarwatse. Tamkar zuciya ta ta tarwatse, tamkar duk achievements dina are nothing because of this. Kamar ni din kaina is nothing tunda har Muhammad ya manta da ni already yayi settling da Safina. Dama haka kishi yake? Lallai na jinjinawa mata masu kishiya musamman idan suna son mijin sosai, Sai da nayi kuka na sosai sannan na dago kai ina kallon sa, fuskarsa tayi ja kamar shi yake yin kukan, muna hada ido ya miko min hankyn daya dauko daga cikin jaka ta da take hannun sa "ya isa haka kar kiyi ciwo kuma. I promise you it is nothing. It doesn't mean anything. I don't know how to explain to you but I promise you zaki fahimta" na karbi hanky din na goge fuska ta sannan na mike tsaye ina jin kirjina yayi min nauyi, ya mike shima sai nace masa in a much calmer voice "you don't have to explain anything. Na riga na fahimta. Ni kadai nake haukana da ma. I ......" Ya katse ni "Piya haukan da nake yi akan sonki na tabbatar yafi naki yawa. Yarinyar can makira ce. She did something. Kuma dama this is exactly what she wanted. This is exactly why she did what she did" na girgiza kaina "I don't want to know what she did or what you did. It is over between us again. I am breaking up with you for the second time" na fada tare da fara kokarin tare taxi, mai taxin yana tsayawa Muhammad yace masa "get out of here, go" mutumin ya bi mu da kallo sannan ya ja motar yayi gaba. Muhammad ya juyo kaina "you are not breaking up with me Safiyya. Never again, I will never let it happen" ya fada with so much confidence, Na juya na cigaba da tafiya tare da cewa "watch me" na cigaba da kokarin samun abun hawa. A lokacin mota ta tsaya a gabana, motar Mustapha, yana zaune a seat din driver fuskar sa cike da alamomin tambaya ya kalle ni ya kalli Muhammad da yake tsaye a kusa da ni hannunsa rike da jaka ta, ya ambaci sunansa "Muhammad?" Muhammad yayi kamar bai ji shi ba, sai ya sake kallo na yace "Mommy tace in biyo ki in kai ki gida, are you coming or not?" Kamar ransa a bace yake amma bani da option dan babu abinda nake so a lokacin irin inyi nisa da Muhammad. Na warce jaka ta daga hannun sa da karfi, karfin da nayi amfani da shi ya sa nayi baya kamar zan fadi, ya saka hannu daya ya tare ni sannan ya mikar da ni tsaye sosai. Ina jin na tsaya nature hannun sa tare da nuna shi "you hurt my heart, you hurt my heart really bad. I don't want to see your face again, ever" sai kuma na zagaya na bude motar na shiga na zauna. Mustapha ya ja muka tafi. Na kwantar da kaina a jikin kujera ina kokarin hana kaina cigaba da kuka, wata irin tafasa zuciya ta take yi. Na rufe ido na ina ta jan numfashi da karfi trying to calm myself amma sai naji Mustapha ya fara magana cikin daga murya "what just happened? What was that? Are you in a relationship with mijin Safina?". Na bude ido na juyo ina kallon sa raina yana kara baci, sai ya cigaba da magana "wancan munafikin yaron. He have been giving Safina trouble all along and now this? Yarinyar nan tana can tana kuka Mommy ta saka ta a gaba ta kasa gane kanta ashe uta ta san abinda yake faruwa, ashe kukan da take yi kenan. What do you think Mommy and Daddy will think idan suka ji wannan labarin?" A hankali nace masa "Mustapha, ko kayi shiru ka daina min hayaniya a kai ko kuma ka yi packing in fita. I don't owe you an explanation. I don't care what you think. am not going to explain anything to you" bai yi shiru din ba ya sake cewa "but you owe our parents explanation na how you are in a relationship with min sister din kj" "step sister" na gyara masa tare da jawo ear piece na saka a kunnuwa na sannan na kwanta a kujerar na rufe ido na, Ban sani ba ko ya cigaba da maganar ko kuma ya hakura, Sai da naji mun tsaya sannan na bude ido na na dauki jaka ta na fito. Shima ya fito yana kallona yace "yanzu ni what do you want me to do with this information" nace "whatever you want. Ko ka wuce ka gaya wa Daddy ko ka koma ka gaya wa Mommy ko kuma ka shiga gidan radiyo ka fada, ko kuma ka rike a zuciyar ka. I don't care", Na juya da sauri na shiga gida, kuma har zuciyar ta wa ban damu ba din. In dai Muhammad ne Safina ta je na bar mata. In dai Safina ce Muhammad yaje na bar masa. Nayi saving Daddy da Mommy stress din solving wannan issue din. Na shiga cikin gidan da sauri, ina jin Esther tana yi min magana ko kallon ta banyi ba na hau sama na tafi dakina na shiga na kulle kofa. Kokari nake vi lallai sai na hana kwakwalwa ta tunanin Muhammad da matarsa, irin abinda na kanyi tun da aka yi auren su, amma kuma yau zuciya ta tayi over powering kwakwalwar ta karbe ragamar controlling emotions dina. Dan haka na zauna a kasa a gaban gado na cigaba da rusar kuka na. My heart was so broken beyond repairs. But my brain was trying to tell me the truth, sai dai zuciyar ta wa taki bata damar yin magana. Sai da na gama sannan na tashi na cire kayan da nayi masa kwalliya da su nayi jita da su a tsakar dakin sannan na saka kafa na tattake su. What was I even thinking? That we will be back together bayan yana auren Safina? Ni kaina na san babu yadda za'a yi Daddy da Mommy su yarda da hakan but I love him so much, yanzu kuma na tsane shi, I hate him so much amma kuma ina son sa, how is that even possible? Him👳🏻‍♀️ Tun da ya dawo baya zama a gida, kamar yadda Abba ya fada aiki ne dankar a office yana jiran sa, ga shi kuma yana so ya fara implementing knowledge din da ya samu a gurin tarukan da yaje, dan haka abu ya taru ya cakude masa. Sai da weekend ya zagayo sannan ya samu hutu ya zauna a gida. But he was being careful yanzu a gida yana kiyaye abinda zai ci ko zai sha ko kuma ma duk abinda zaiyi amfani da shi. Shi gani yake yi asiri Safina tayi masa da ya saka shi acting that way a daren can. Wannan ya sa kofar part din sa yanzu kullum a rufe take, yana shiga zai rufe ta ciki, in ya fita ma kuma ya rufe ya tafi da key din. Yanzu ko abincin da take ajiye wa kullum ba ta da damar ajiyewar. A ranar Saturday din ne ya samu ya kwanta yayi bacci mai nauyi sosai da rana. Sai da zuhr ya tashi, ya shiga toilet yana wanka yana gab da fitowa yaji wayarsa tana kara, ya gama ya fito ya duba sai yaga Mama ce ta kira shi. Ya na kokarin kiran ta kenan sai ga wani kiran ya shigo, ya dauka ta tambaye shi a ina yake sai ya gaya mata yana gida, nan take ta hau shi da fadan wai ana ta nemansa a gidan ya rufe kofarsa, he tried to explain to her bacci yake yi amma taki sauraren sa tace maza ya je ya gaishe da Mommyn Safina tazo tana neman sa. Da sauri ya zura riga ko gama drying jikinsa bai yi ba ya fita dan da gaske ya ji Mama ta dau zafi. Sai dai yana shiga falon Safina ya ganta, ba Safina ba Safiyya. She looked different, more matured but more beautiful. Amma kuma hankalin ta a tashe yake, ranta a bace yake, and he was more concerned about abinda ya bata mata rai ya tayar mata da hankali haka then fadan da yaji Mommy ta fara yi masa. Bai ma ji me take cewa sosai ba, kamar dai she was showing dissatisfaction akan yanayin zaman su da Safina har tana magana in baya son ta su suna sonta, But then he heard something. "Ga Safiyya nan da auren ta ya mutu babu abinda ya same ta" and it caught his attention, a take kuma ya gane me hakan yake nufi. Auren Safiyya ya mutu. As he was trying to assess the situation sai ya ga Safiyya ta bar inda take tsaye tayi hanyar waje da sauri, and bai tsaya cigaba da jin fadan da ake yi masa ba ya mike shima da sauri ya bi bayan ta yana kiran sunan ta. Har waje ya bita taki kula shi, daga baya kuma sai ta gaya masa abinda ya bata mata ran, his worst nightmare, maganar cikin Safina. Tabbas maganar ta bata mata rai sosai and she cried like a baby. She sat down on the floor a bakin titi and cried. Wannan kukan nata ba karamin kona zuciyar sa yayi ba. Ya rasa mai ze ce mata. Yasan zai iya yi mata bayani amma kuma ba zai iya ba. To me zai ce? Ya rasa menene ya fi daga masa hankali yanzu, the fact that matar da baya so is pregnant for him or the fact that matar da yake so is crying because of him. Yayi kokarin yi mata magana ya kasa, yayi kokarin lallashin ta amma bai san kalaman da zaiyi amfani da su ba. So he just sat with her and wished he can cry with her. A karshe dai ta gaya masa maganganun da suke nuna zurfin bacin ranta sannan tace masa "I am breaking up with you again". Amma duk ba wannan ne damuwar sa ba, damuwar sa shine Mustapha da yazo ya dauke ta a mota suka tafi. Ya tsaya yana bin motar da kallo, and the first thing that came to his mind was ranar da suka yi haduwa ta biyu a duniya, ranar da Mukhtar ya zo ya dauke ta a mota suka tafi, she later married Mukhtar. Ya girgiza kansa a hankali yace "no…..no. not this time. Not again" ya juya da sauri ya koma cikin gidan sa sannan ya shiga part din sa da sauri totally forgetting about the problem with Safina and Mommy. Shi kawai abinda yake ransa shine Mustapha da Safiyya a mota. She is broken. She may even open up to Mustapha and give him a chance to lallashe ta. Ya sake girgiza kansa da sauri "uhm uhm" wannan rarrashin shi zai yi shi tunda shine yayi wannan laifin. Frantically yake neman key din motar sa, totally forgetting cewa yana kan abinda aka tanada musamman dan ajiye car keys a palon sa, sai daga baya kuma ya tuna sannan ya tafi da sauri ya dauka, Unlike before yanzu ai ya san gidan su, ya san har falon Daddy. Wayar sa ce tayi kara a cikin aljihunsa. Ya saka hannu ya dauko ta and he saw sunan Mama. Yaji gabansa ya fadi, sai a lokacin ya tuna da inlaw dinsa da ta kira shi tana yi masa fada. Yaji kamar kar ya dauki wayar. Allah ka dai yasan abinda suka kira suka gayawa Mama. Wannan wanne irin kaddararran aure ne? Amma kuma ba zai iya barin Mama tana kiran sa bai dauka ba. Tafi karfin haka a gurin sa. Yayi sliding wayar ya dauki kiran ya saka a kunnen sa "hello Mama" ya saurara yaji ta fara yi masa fada amma sai yaji tace "kaje ka gaishe ta?" Yace "eh naje, har na fito ma" tace "kana ina yanzu?" yace "ina daki na" tace "okay ka 2o ka same ni a gidan Mommy" daga nan ta katse kiran. Ya rike wayar a hannunsa yana jujjuya ta. Shi kukan Safiyya kawai yake tunawa. So yake yaje yace mata "I am sorry" but sorry for what? Ya kawar da maganar daga zuciyar sa sannan ya fara kokarin chanja kayansa, Shi dai ya san indai har maganar gaskiya za'a bi bai aikata laifin komai ba ballantana ya bada hakuri, amma ba maganar gaskiya ake yi ba, maganar Safiyya ake yi. And as far as magana ce a tsakanin sa da Safiyya then she is always right. Kuma zai bada hakurin ko da kuwa cikin charbi ne. Ya gama chanja kayan ya dauki key din mota ya fita, sai da ya kunna motar sannan ya yi tunanin dolen sa a yanzu gidan Mommy zai je gurin Mama, sai dai yana fatan gain maman ba zai dauki lokaci ba. Ya na tuki yana tunanin maganganun Safiyya, she said she is going to break up with him, amma shi dai ya san dama they broke up already, bai kuma san sanda suka dawo ba ballantana har su sake wani breaking up din. Kukan ta tabbas ya tayar masa da hankalin amma kuma a wani bangaren ya kwantar masa da hankali ne saboda ya tabbatar masa da matsayin sa a gurin ta and yayi boosting confidence din sa. Ya tuna kalmomin ta "ashe ni kadai nake haukana" and he smiled tare da sauke ajjiyar zuciya. Whether she have been with Mukhtar or not, shi dai abinda ya fahimta shine yana cikin zuciyarta kamar yadda take cikin ta shi. And that is all that matters. Sai da ya tsaya yayi sallah a masallacin kofar gidan sannan ya shiga cikin gidan, ya ga motar Mammy ya san tana ciki ita ma, dama al'adar su ce sukan je gidan Mommy duk Saturday su yini tare da ita. A falo ya tarar da Mammy ita kadai tana kallon tv, tayi murmushi tana kallon sa "ubana maganin kuka na" ya yi mata murmushin shima sannan ya karasa ya gaishe ta. "Kai yanzu tunda kayi aure kuma shikenan an daina gain ka, matar kata boye ka a gida" yayi saurin kare kansa "Mammy wallahi aiki ne ya sako ni a gaba. Abba sam baya daga min kafa. Shi yasa dama tun farko na gudu daga gurin sa na tafi MD" tace "haka ne. We are all proud of what you have achieved so far. Allahu yayi jagora" yace "Ameen" sai ta nuna masa dakin da yake kusa da gurin tace "mamanka tana ciki tana Sallah. Maybe ta idar" ya mike ya shiga dakin da ta nuna masa. A ciki ya samu Mama ta idar da sallah tana addu'a. Ya zauna yana jiran ta sai da ta shafa sannan ta juyo tana kallon sa, ya gaishe ta "Mama barka da rana" bata amsa ba sai ta cigaba da kallon sa, ya san irin wannan kallon and it made him nervous, sai a karshe tayi magana and she asked exactly abinda ya san zata tambaya "me yake damunka?" Ya danyi dariya nervously "Mama babu abinda yake damuna fa, stress din aiki ne" ta cigaba da kallon sa "kun yi fada da Safina ne? I don't like the tune of her mother sanda ta kira ni dazu" ya girgiza kai "babu abinda ya faru Mama. Su suna da kananan maganganu ne kawai. Dan Allah kar kike biye mata in ta gaya miki abu har ki bata ranki" ta dauke idon ta daga kansa tace "in ba fada kuka yi ba to wani abun ya faru da ban. Me ya faru?" Ya gyara zamansa, she will not let the issue go. Yace "Mama, even if I tell you yanzu ba zaki gane ba, zaki damu ne kawai. I will tell you sanda na zama confidence cewa zaki fahimce ni kuma ranki ba zai baci ba" ta juyo tana kallon sa tace "okay kai ka fahimta amma ni ba zan fahimta ba?" Ya girgiza kansa "ba haka nake nufi ba. Ni kaina ban san stand dina akan maganar ba, I just don't want to worry you for nothing. Nima ban fahimta ba ballantana in fahimtar da ke" ta dan vi shiru sannan tace "shikenan. Allah ya jishe mu alkhair'" yace "Ameen" suka dan yi hirar gida kadan sannan tace mass yaje ya gaishe da Mommy (his grandma). Ya shiga dakin ta ya tarar ita ma ta idar da Sallah tana kokarin fitowa, sai ta koma ta zauna tana yi masa murmushi "mai gidan katako" yace "na karfen dai, Ya Amen ne na katakon ai" tace "duk daya, Da kai da shi duk babu wanda yake yi min cefane dan haka duk na katako ne a waje na. Na karfe na yana aljanna" ya durkusa a gaban ta "barka da yamma" ta shafa kansa tare da amsawa cikin sakin fuska "ina amaryar ka? Tun da tazo ranar nan ba ta kuma dawowa ba. Ko ba ka koya mata zumunci ne?" Yayi murmushi bai ce komai ba sai ya fara kokarin mikewa, shi duk hankalin sa yana kan Safiyya, ko ta daina kukan? Har ya mike sai Mommy tace "mamanka ta gaya min ashe Safina jikar Hajiya Maryama ce, matar Alhaji Nasiru" ya juyo yana kallon ta yace "ba jikar ta bace ba, yar kanwar ta ce, but kanwar a hannun ta ta tashi shi yasa ake dauka jikar ta ce" ya gyada kai cikin fahimta, har ya sake juyawa sai tace "har na dauka yar Safiya ce" yaji gabansa ya fadi, ya juyo yana kallon ta yace "Safiya?" Tace "eh safiya, akwai yar Maryama sunan ta Safiya, very beautiful girl, sun taba zuwa gidan nan shekaru da yawa da suka wuce tare, lokacin duk iyayen ka suna makaranta, har nake cewa ta bani ita in samo mata miji a Nijar sai tace min an saka ranar ta a lokacin, da wani mai suna Adam". Ya juyo da baya kamar wanda ake ja da igiya ya dawo gabanta "Safiya kika ce Mommy are you sure? Kuma Adam zata aura?" Ta bata rai "me kake nufi ne wai? Na gaya maka sunan yarinyar Safiya kuma zata auri Adam sanda suka zo and you are still asking me?" yace "I mean shekarun da yawa, are you sure about the names? Saboda Hajiya Maryama bata taba haihuwa ba" ta harare shi "shekaru da yawa? Ni fa nonon rakumi na sha while growing up ba processed milk irin wacce kuke sha yanzu ba. My memory is very good. Safiya sunan ta. Kuma Maryama tace min yar ta ce, wanna shine abinda na sani" Sanda ya shiga mota ya fara driving sai yaji ya kasa tantance wanne tunanin ya kamata yayi yanxu. Safiya matar Adam will definitely mean mahaifiyar Safiyya. In dai kuma ba wani babban coincidence ba. In haka ne akwai dangantaka ta jini kenan tsakanin Safiyya da Safina? Ya tuna maigadin gidan su Safiyya ya taba gaya masa cewa tun mahaifiyar Safiyya na da rai Mommyn Safina take zuwa gidan gurin ta amma bai san dangantakar su ba. Are they related? Direct gidan su Safiyya ya tafi. Shi yanxu yasan yana da license din shiga gidan a matsayin sa na mijin Safina, Sai dai kuma bai san abinda zai ce ya samu ganin Safiyya ba musamman tunda fushi take yi da shi sosai kuma ba lallai ne ta bashi hadin kai ba. Kuma yana tsoron kar ace Mommy ta dawo gida dan kar ta sake yi masa hayaniya a tsakiyar ka. And that guy Mustapha ya gansu tare kuma bai san kallon da yayi wa abin ba. Dan haka dole ya zama careful kar ya bata goma daya bata gyaru ba. Mai gadi yana ganin sa ya tafi da niyyar bude masa kofa amma sai yayi masa alama da yazo, ya fasa bude kofar ya taho gurinsa sai ya tambaye shi "Safiyya tana gida?" Baba Ya'u yace "a'a sun fita da su Hajiya da farko, sai kuma suka dawo tare da Mustapha, daga nan kuma sai na ga ta fita ita kadai, ban san inda taje ba". Muhammad yaji babu dadi. Ya sake tambaya ko ita Mommy ta dawo sai mai gadin ya ce masa bata dawo ba, Mustapha ma kuma ya sake fita. "Kamar gidan ka naji ance sun tafi ai", Daga nan dai sai ya shiga gidan yaje ya gaishe da Daddy, bai ji dadin gain jikin sa ba but yaji dadin gaishe shin da yayi da kuma yar maganar da suka yi, sai dai a cikin sauri yayi ya gama dan baya son Mommy ta dawo gidan ta same shi ba tare da ya samu Safiyya sunyi magana ba dan bai san zuwa yanzu abubuwan da Safina ta gaya wa Mommy din ba. Bai kuma san me zai ce da Daddy ba a yanzu ba tare da ya yi magana da Safiyya ba. A haka dai ya hakura ya fita daga gidan thinking of a way da zai samu ganin Safiyya ko kuma at least yayi waya da ita. Yanzu ko number din ta bashi da ita a wayarsa and even if he is to get the number ya san tayi blocking dinsa months ago dan haka ko ya kira ba lallai ta shiga ba. So he got another sim card just in case. Bai koma gida ba sai very late, ya san dai dole Mommy ta bar gidan a lokacin. Ya shiga part dinsa ya rufe kofa kamar kullum sannan ya hada tea ya sha yayi wanka yayi shirin kwanciya bacci. Ya kwanta akan gado rigingine yana kallon ceiling, idanunsa babu bacci ko kadan a cikin su, babu abinda yake gani a cikin su din sai fuskar Safiyya tana kuka, babu kuma abinda yake ji a kunnen sa sai muryarta tana kuka. Ya jima a haka sai ya mike tsaye ya dauki wayarsa ya fita da sauri ya shiga part din Safina. Dakin da yasan tana kwana a ciki ya dosa kai tsaye, ya je ya tura kofar ya shiga, har ta kwanta dan dakin da duhu babu fitila. Ya kunna fitilar dakin. Tana kwance akan dago ta rufa da bargo, ta juyo da sauri tana kallon sa, daga alama ta kwanta ne kawai amma ba bacci take yi ba. Ta mike zaune da sauri tana kallon sa idanunta cike da mixed emotions, akwai toro a cikin su dan har lokacin bata manta da ranar nan ba, akwai kuma anticipation and hope din cewa ya dawo ne for more. Kirjinta yana bayyana cika da kuma firmness irin na masu ciki. He looked so manly in his armless rigar bacci mai hade da gajeren wando iyakacin guiwa. Ya karasa bakin gadon da take kwance akai ya dora kafarsa daya akai yana kallon ta cikin ido yace "bani wayarki" she looked confused "me zaka yi da waya ta? Na rantse babu komai a cikin ta. Me aka ce maka navi kuma?" Ya mika mata hannun sa '"bani wayarki nace" ta jawo wayar a gefen pillow din6ta ta mika masa "wallahi babu komai a ciki. Kuma ka duba ka gani" ya karba ya jujjuya ta sannan ya mayar mata da ita yace "bude ta" ta bude ta sake mika masa with confidence dan tasan ita dai bata da wani abun boyewa a cikin wayar. Ya dan jima yana daddanna wa sai kuma ta ga ya dauko tasa wayar ya daddanna ita ma, and she realized abinda yayi, and her heart breaks to thousand pieces. Yana gama wa ya jefa mata wayar kusa da ita ya juya zai fita, cikin karyayyiyar murya tace "me kayi? Me ka dauka a cikin wayar ta wa?" Ya juyo yana kallon ta yace "number din Safiyya" sannan ya juya ya fita, ya bar mata kofa a bude fitila a kunne. Direct ya koma dakin sa ya dauko sim din da ya siyo dazu ya saka a cikin wayarsa, yayi recharging sannan ya koma ya kwanta yana kallon ceiling kafafuwan sa a kasa yayi dialing, not even considering how late it is. Ta shiga, har ta katse bata dauka ba and he called again, tana cikin ringing ta dauka kuma daga muryarta ya san ba bacci take yi ba "hello? Who is this?" Ya lumshe ido yana jin yadda zuciyar sa tayi contracting, he so much misses jin muryarta over the phone and the memories of all those late night phone calls just came flooding back to him, Ta sake yin magana "hello? Waye wai?" Yayi magana a can kasan makogwaronsa "sunana Muhammad Gidado, Please don't hang up" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Fifty: Breaking News Yaji tayi shiru daga can barin, amma kuma ya san ta ji shi sannan ta gane cewa shine. Yace "kiyi hakuri na kira ki cikin dare, but na kasa bacci ne, ba zan iya bacci ba without at least talking to you. I tried seeing you ban samu ba. Dan Allah ki bani dama muyi magana". Tace cikin dacin murya "babu wata magana a tsakanin mu Muhammad, kai mijin yayata Safina ne, kuma ban yayan ta, wannan shine kawai alakar da take tsakanin mu. Bayan wannan ban san wata da har zata hanaka bacci ba" yace "naji. And ina so ki sani na shirya jin duk abinda zaki fada min as long as zaki saurare ni nima. Yanzu dai tambaya daya nake ©️2 neman alfarmar ki amsa min, just one question, koma menene zai biyo daga baya" bata ce komai ba amma kuma bata katse kiran ba, sai yace "dazu naji Mommy tayi wata magana, tace auren ki ya mutu, I want to know idan da gaske ne, I want to make sure dai dai kunne na yaji min ba wai ya gaya min son raina ba ne ba" tayi shiru bata amsa masa ba. Ya sake cewa "Piya, please ba dan hali na ba l want to confirm from you, this is very important, bana son in dawo da tunanin ki cikin zuciyata, bana so bakina ya furta kalaman da suke cikin zuciyata akan ki alhalin kina matar wani, bana so in yiwa Allah laifi, dan Allah ki bani amsa". Ta sake yin shiru, sai da ya kara roka "Piya Please!" Sannan tace "aure na ya kare da Mukhtar, but that does not mean anything. Now this is a warning, kar ka sake kira na" daga haka ta katse kiran. Ya dora wayar akan kirjinsa lips dinsa suna curving into a wide smile, "alhamdulillah" ya ambata, shi yasan second chance ne Allah ya bashi at happiness kuma ba zai taba yin wasa da wannan chance din ba, zai yi fighting for his happiness with everything da yake da shi a duniya, Ya san dai abin ba mai sauki bane ba, musamman considering dangantakar matarsa da Safiyya, both iyayensu ba zasu yarda ba, Safina also will do everything in her power ta hana abin kasancewa but ba ita ce damuwar sa ba. Damuwar sa a yanzu shine yadda zai yi convincing iyayensa da kuma Daddyn Safiyya. Yayi ta bitar abubuwan da suka faru a ranar a cikin kansa, musamman maganganun Safiyya na dazu da kuma na yanzu, yasan cewa ranta a bace yake sosai kuma bai yi blaming dinta ba for that, amma kuma sam kalamanta basu bata masa rai ba sai ma sanyaya masa zuciya da suka yi, saboda dukkan kalaman nata were screaming "I love you" shi kuma wannan wan security ne a wajen sa ya san space dinsa yana nan a cikin zuciyarta. Abinda ya rage masa shine ya samu ta huce daga fushin da tayi and then the battle will begin. Ya jima a haka yaji karar shigowar message wayarsa, zuciyarsa ta harba da sauri, ko bakar magana zata turo masa indai har ta turo din to wani step ne for him. Amma yana daga wayar sai yaga Safina, yayi dan karamin tsaki sai kuma ya karanta sakon nata. "Just for the records, ban taba yin nadamar wani abu ba a rayuwata kamar yadda nake nadamar auren ka a yanzu. Ban taba ganin azzalumin mutum, mugu, wanda bai damu da kowa ba sai kansa ba a rayuwata irin ka. I have been saying na yafe mata dukkan abubuwan da kake yi min da saboda wadannan tsakani na da kai ne, amma wanna ban yafe ba tunda saboda wata ne, ban yafe ba kuma sai Allah ya saka min" Har ya ajiye wayar ya fara shirin yin bacci sai kuma ya dauka ya tura mata reply. "You are mistaken, it has always been because of her, da ace baki ci amanar ta ba, da ace baki yi min karya a kanta ba, I might have been the best thing that happened to you" Tun daga lokacin Muhammad ya daura damarar dawo da matsayin sa a gurin Safiyya amma abin yana neman ya gagare shi. Tun ranar da suka yi waya da ya tashi da safe ya kira ta sai yaji ta rufe sabon layin nasa shima. Bai hakura ba haka ya cigaba da siyan layuka tana kuma rufe su da zarar ta fahimci shine, daga baya kuma sai ta daina daukan kiran ma kwata kwata, maybe tayi deciding ta daina daukan new numbers saboda shi. Messages kuwa babu ta hanyar da bai tura mata su ba har ta e-mail din ta amma babu reply, bai ma sani ba ko tana gani ko kuma bata gani amma haka ya cigaba da tura mata su kullum safe da rana da daddare kamar shan magani. Yayi zirga zirga zuwa gidan su yafi adadin da zai kirga amma baya samun gain ta, lokuta da dama tun daga gate mai gadi yake gaya masa bata nan, wani lokacin kuma ya samu ya shiga sai ya kare da gaishe da Daddy amma ba zai ga Safiyya ba. Daga baya ma da yaje sai mai gadin, wanda zuwa yanzu ya fara yi masa wani irin kallo saboda yawan tambayar Safiyya da yake yi, ya gaya masa cewa Safiyya ta tafi Umrah. Babu abinda kuma ya rage masa yayi illa ya jira ta ta dawo, while jiran kuma ya cigaba da tura mata messages telling her every detail about his days da kuma halin da zuciyar sa take ciki akan soyayyar ta. Duk da bashi da tabbacin tana karantawa or not. Har da bata sakon tsarabar da zata taho masa da ita daga Saudiyya, wani turare da ta taba kawo masa wani zuwa da tayi lokacin suna tare. Ya lura cewa Safina ta zama bitter a cikin yan kwanakin nan, har tsayawa ta kanyi a waje ta jira shi ya dawo da daddare ta tambaye shi daga ina yake. Ko kuma in taga yana waya ta tambaye shi da wa yake waya, shi har dariya ta kan bashi idan tayi masa irin wannan tambayar, baya kuma bata lokacin sa gurin bata amsa. A cikin lokacin ne Humaira matar Al'ameen ta haihu, ta haifi baby boy. Tun a asibitin da ta haihu da shi aka yi komai har aka sallame ta ta dawo gida sai kuma Mama ta matsa masa tace ya dauki Safina ya sayi kayan babies ya bata suje tare ta kaiwa Humaira. He did that, duk da cewa zuciyar sa bata so amma baya tsallake maganar Mama dan haka yaje ya hado kayan babies masu kyau ya zo ya dauki Safina a mota suka tafi gidan Al'ameen. Ya dauka zata yi masa surutu yauma irin wanda take yi masa a duk chance din da ta samu amma sai ya ga ko kallon sa bata yi, wayarta kawai take danna wa, wannan ya bashi damar driving din sa hankali kwance har suka je gidan. A bakin gate yayi packing, sannan yace mata "ga kayan barka nan a baya, ki dauka ki shiga ki kai musu" ta juyo da sauri tana kallon sa '"ba tare zamu shiga ba? Mama tace min zaka kaini inyi barka" ya daga kafada "kuma na kawo ki ba, Ga gidan nan. Suna ciki. I guess akwai mutane sosai ma a ciki duk sun sanki har ita mai jegon in ke baki san su ba. Just go……. In na gama abinda nake zan zo in dauke ki". Ta bude kofar ta fita reluctantly sannan ta bude baya ta dauki ledojin da ya ajiye a ciki, yayi murmushi mugunta, ya san tana avoiding shiga family dinsa tun ranar da ya kaita gidan kakannin sa and yanzun ma yasan gidan Al'ameen din a cike yake da yan barka. Bai dawo daukan ta ba sai dare, and sanda ya zo daukan ta tana shiga motar ta fara kuka, ya mika mata tissue box and she cried har suka je gida. Her🧕🏻 Ranar da muka je gidan Safina Bayan na gama kuka na a daki sai kuma wani tunani ya zo min, na san yadda naga Muhammad dazu akwai yiyuwar zai iya biyo ni gida and zai iya yin dabara irin ta ranar nan yaje wajen Daddy ya saka Daddy ya kira ni, pretending zai bani sako or something. Ni kuma idan akwai abinda bana son yi a yanzu to shine ganin sa. Wannan ya sa na tashi na share hawaye na na sake fita na tafi inda a can ne yanzu na ke samun solace, the oasis, ina fita da mota naga guards dina sun biyo ni and I felt safer with them, ko ya biyo ni zasu hana shi karaso wa inda nake, A Oasis na wuni ni kadai, har sai da naji an fara kiran magrib sannan na sake dauko mota na taho gida, na san Daddy ba zai neme ni ba tunda ya na tunanin muna tare da Mommy a gidan Safina, amma kuma tunani na shine abinda ya faru a gidan Safina din bayan ni da Muhammad mun fita, me Safina tace wa Mommy? Na dai ji Mustapha a cikin maganganun sa ya ambaci cewa Safina tana gida tana kuka, na kuma san yadda Mommy take son yayanta zata saka ta a gaba ne da tambayar abinda ya saka ta kuka, and I definitely know Safiya will lie and make my the villain. Ina dawowa gida na tarar har lokacin su Mommy basu dawo ba, na shiga gida na wuce dakina nayi alwala na fito kenan zan tayar da naji shigowar su Mommy, na tayar da sallah ta, sanda na idar sai na zauna akan sallaya ta for the first time na rasa addu'ar da zanyi, gani nake na rasa Muhammad, and with him na rasa komai da nake aiming for a rayuwa ta. Duk wani hope for a brighter future da naji sanda na rabu da Mukhtar naji ya tarwatse a zuciya ta. Ina nan zaune akan sallaya ina aikawa da annabin tsira salati sai naji an bude kofar dakina an shigo, na daga kai na ga Mommy ce da alama ko cire mayafin ta da ta je gidan Safina da shi bata yi ba. Ta shigo ta zauna akan kujera tana kallona har na shafa addu'a ta sannan nayi mata sannu da zuwa. Tace "ya ciwon kan naki?" Nace da sauki. Sai ta sake cewa "dazu kuma da kika ji kan ya dame ki maimakon ki sha magani ki kwanta a can sai kika fito ke kadai zaki taho gida? Kamar wadda taje bakon guri? Gidan yar uwarki ne fa, gidan Safina ne fa" na tashi daga kan sallayar na fara ninke hijab dina nace "Mommy nafi relaxing ne a gida, shi yasa" ta danyi shiru tana kallona sannan tace "sanda kika fita kun hadu da Muhammad?" Na dauke kai ina nade sallaya nace "wanne Muhammad?" Tace "'kin san muhammad din da nake nufi ai, mijin Safina" naji ciwon kalmar mijin Safinan amma na danne nace "a'a, neman shi ake yi?" Tace "sai naga kamar ke ya bi sanda kika fita yana kiran sunan ki. Na dauka zai dawo dake ne yace ki sha magani ki kwanta kuma naji ku shiru, shine na tura Mustapha yabi bayan ku in kin ki dawowa ya dauko ki ya kawo ki gida, shima kuma da ya koma na tambaye shi Muhammad din sai yace bai ganshi ba" na ajiye kayan sallah ta a inda suke na rufe ban ce mata komai ba, Sai ta nuna min kusa da ita a kan kujerar da take tace "zo ki zauna" na je na zauna kamar yadda tace na sunkuyar da kaina kasa ina kallon yatsun hannuna. Tace "Safiyya, Yar war ki Safina tana cikin matsala sosai a gidan mijinta. Allah ya jarabce ta da auren mijin da bai san darajar ta ba ko kadan ballantana ta iyayen ta. Tun kafin bikin su na fahimci haka, amma rabon zata sha wahala da kuma rabon cikin da take dauke da shi a yanzu ya saka ban yi kokarin tsayar da auren ba sai nayi tunanin miskili ne kawai amma zata shawo kan shi. Sai bayan da aka daura auren sannan take gaya min gaskiya, ashe a social media ta ga hoton sa ta kamu da son sa, sai ta nemi kanwar sa ita kuma ta hada ta da shi. To coincidentally sai ya kasance a lokacin su kuma iyayensa suna son yi masa aure, watakila da ma kokarin fin karfin su suka ga yana yi shine suke neman yarinyar da zasu manna wa, ita kuma Safina rabon shan wahala ya kai ta". Tayi shiru tana kallona, maybe tana jira ne in ce wani abu, jin ban ce komai ba sai ta cigaba "ni abinda yafi bata min rai shine idan da yasan baya son ta ai da sai ya fada, tunda na tabbatar iyayensa ba zasu yi masa dole ba, amma sai ya karbi auren yarinyar nan, ita kuma Safina munafuka tunda ta san daga ni har Daddyn ku ba zamu yarda da irin wanna auren ba shine ta kai shi Katsina, su kuma wasu munafukan, dama ba sonta suke yi ba ba damuwa suka yi da ita ba shine basu à tsaurara binciken komai ba dan sunga mai kudi ne suna saka ran zai ke kai musu wani abu, basu san cewa ita kanta Safina ba abinda take samu daga gare shi balantana su, shine suka daura mata aure da shi" ta sake yin shiru,na dago kai in kallon ta nace "Mommy why are you telling me this?" Tace "why not? Me yasa ba zan gaya miki ba kuwa Safiyya, saboda yar uwarki ce ita, ina ganin ya kamata ace kin san halin da take ciki, kuma ai hausawa sunce ciwon ya mace na ya mace ne. Na tabbatar ba zaki so Safina ta kasance cikin kunci a gidan mijinta ba ko?" Ban amsa tambayar tata ba sai nace "Mommy yanzu ni me kije so inyi akan hakan?" Tace "you are very smart Safiyya, in fact ni ban taba ganin someone as smart as you ba, kin san Safina bata da yawo sam, so nake ki saka kanki in her shoes kiyi tunanin me take ji a zuciyar ta sannan idan ke ce me zaki yi a kai. Sai ki bata shawara, na tabbatar in tabi shawarar ki zata samu waraka" na cigaba da yin shiru, sai ta mike "kinji kamar har an fara kiran sallar isha, bara in sauri inje inyi Sallah, just think about it Safiyya, na san zaki samo mata solution. Tayi kuskure na sani, amma yanzu it is too late to go back a gyara kuskuren tunda already har an fara hada zuriya. So nake muyi standing together as a family mu taya ta gyara gidan ta, kamar yadda muka yi standing together as a family muka rufe maganar kaddarar data same ki". Ta juya, har ta kai bakin kofa sai ta kara tsayawa tace "in kin gama ki sauka muci abinci tare. Sai mu bawa Daddy labarin gidan Safina". Ta fita tare da rufe min kofa. Na bi kofar da kallo sannan na dawo da hankali na kan yatsun hannuna naci gaba da kallon su, na tabbatar Safina ta gayawa Mommy wani abu a kaina ni da Muhammad, kuma na tabbatar ba gaskiya ta gaya mata ba. Dan wadannan maganganun nata a cike suke da harshen damo, she meant more than she said. Har da gori a cikin maganar and I also felt a threat a karshen maganar ta lokacin da ta ambaci Daddy. Na tashi na sauka kasa, na tarar Esther tana ta hidimar shirya dinning sai na taya ta, nayi kokarin yi mata hira to make up for dazu dana ni ignoring dinta tana y min magana, nace "Esther ya kamata a samo wadda zata ke taya ki aikin gidan nan gaskiya, aikin yana yi miki yawa, dama mun barki ke kadai ne saboda ba zama muke yi a gidan ba yanzu kuwa naga Daddy kamar yafi jin dadin zama a gidan nan dan haka bansan sanda zamu koma Kano ba" ta bude ido "wata kuma Madam? No dai a bar ni ni kadai. Nafi jin dadin aikina ni kadai bani da wani problem. Ana kawo Wata zamu fara competition for your appreciation. Ni ina da kishi sosai. Idan something nawa ne nafi son ya zama nawa ni kadai" nayi murmushi "that makes the two of us Esther. Tace "I think that makes almost everyone. Kowa yana da kishi. Maza da mata. Na wasu ne kawai yafi na wasu, wasu suna fitowa da shi fili was suna boyewa. Ya danganta da halin mutum". Na tayata ta karasawa Daddy soup din da ta hada masa, saboda yanzu baya iya cin solid food irin namu, soup ce da aka yi da shredded chicken, shredded Irish potatoes and shredded vegetables aka kuma dafa su sosai yadda ba zasu bawa cikin sa wahala wajen digesting ba. Shi ya fara zuwa dining din kuwa a kan electronic wheelchair dinsa, naje ina kokarin gyara masa zamansa sai ga Mommy ta sauko sannan sai ga Mustapha shima ya shigo, na zauna tare da su muka ci abincin trying as much as I can inga cewa na danne abinda yake zuciya ta amma da kyar nake samo lomar tuwon da nake ci take wucewa. I expected Mommy ta bawa Daddy labarin abinda ya faru a gidan Safina ko tayi complain akan halin mijin Safina amma sai naji bata yi ba, sai labarin abincin da Safina ta dafa musu ta bayar "yarinyar nan bata iya girki ba. Suma yaran da na kai mata duk basu iya ba ashe. Nace wanna wanne irin kwamacala kike baya mijin naki? Kuma wai a haka ta shiga online classes na koyon girki, daga videos din take kalla tana yi". Mustapha yayi gyaran murya yace "gwara dai a samo mata wadda zata koya mata girkin har gida, tun kafin masu iya girki su kwace mata miji" ya karasa maganar yana kallona. Daddy da yake jin su yana murmushi yace"ai kuwa dazu mijin yazo gidan nan kafin ku dawo" duk muka juya muna kallon sa, ya cigaba da magana fuskar sa dauke da murmushi "yaron kirki ne. Yazo ya gaishe ni. Yace ya ga kunje amma babu ni shine yace bara shi yazo ya duba ni" Mommy tace "what? Lallai munafunci ba'a mata kawai ya tsaya ba" Daddy ya kalle ta yace"me yasa kika ce haka?" Ta girgiza kai tare da cigaba da cin abincin ta amma kana gani kasan ranta ya baci tace "babu komai, wata maganar ce daban". Ranar da daddare ban iya bacci ba kamar yadda nayi tunani, babu abinda kwakwalwa ta take yi min tunani sai Muhammad da Safina, ko me suke yi yanzu? Na tabbatar suna manne da juna. Munafiki, da rana zai wani ringa nuna wa duniya kamar baya son ta da daddare kuma yaje yayi mata ciki. Ina nan kwance in da dark, trying to get rid of tunanin Muhammad da matarsa sai naji wayata tayi kara, na dauka na ga bakuwar number and the first thing that came to my mind shine Muhammad ne. Shine ya saka sabon sim ya kira ni dan yasan nayi blocking wadancan. Na rike wayar ina kallon ta har ta katse, amma kuma ji nake zuciya ta tana bugawa har a cikin makogwaro na. Nayi missing din sa sosai, nayi missing our long night calls da bamu da mu da nisan da dare yayi ba. Nayi missing listening to his deep calming voice. A lokacin wani kiran ya sake shigowa, kwakwalwa ta tana gaya min inyi ignoring ko in kashe wayar ma gabakidaya but my heart wants to listen to his voice again, And I followed my heart, na dauka, pretending ban san cewa shine ba "hello, who is there" yayi shiru, sai kuma naj haushin kaina, wata kila ma bashi bane ba, to ya ma za'ayi ya kira ni a wannan daren bayan na san yana can manne da matar sa? Har zan katse kiran sai kuma naji muryar sa "sunana Muhammad Gidado, Please don't hang up" and all the emotions and the memories came flooding back to me. He sounded just like when we were free and without a problem, kamar babu abinda ya chanja, yet everything has changed. Misali matar shi da take kwance maybe ma a kusa da shi a yanzu, watakila ya gama lallabata ne ta bata hakurin dazu, tayi bacci shine zai kira ni, watakila ma satar jiki yayi ya fito daga dakin su yaje waje ya kira ni. Wadannan thoughts dinne suka sa na katse kiran bayan na tabbatar masa da rabuwa ta da Mukhtar kuma na tabbatar masa da cewa babu sauran change of something between us. Ina katse kiran kuma nayi blocking number din ita ma. Yaje ya karata da Safinar sa na bar mata shi A daren na fahimci cewa rayuwa zata karayi min tsananin a garin Abuja, sai nayi tunanin alkawarin da nayi wa Hajiya na zuwa Umrah daga ni sai ita, ina ganin lokaci yayi da zan cika mata alkawarin ta. Washegari da naje gaishe da Daddy ma gaya masa plan dina, ya amince kuma ya nuna jin dadin sa sosai, nan take kuma ya kira wani agent da zaiyi mana shirin komai. Sai kuma yace "in kun dawo kuma sai mu shirya muje gabakidaya da Sa'adatu da yara" nayi shiru ban ce komai ba, sai ya kira sunana "Safiyya" na dago kai ina kallon sa amma ban amsa ba sai yace '"koma menene a tsakanin ki da Sa'adatu da yaranta ki ajiye shi a gefe, na dauka maganar zargin da kike wa Mustapha ne ya saka ki ke jan jikin ki daga gare su, yanzu wancan issue din is over but har yanzu you seem even more distant than before. Akwai wani abun ne?" Na sunkuyar da kaina kasa ina girgiza shi sannan nace "babu komai" yace "okay. Bana son a samu komai din, bana son wani issue tsakanin ku because without Ahmad, yanzu su ne kadai dangin da kike da su a duniya". Na tashi kenan zan fita sai ga Mustapha nan ya shigo, ya gaishe da Daddy nima sai na gaishe shi, zan fita kenan yace min "zaki je Oasis ne yau Fiyya? In zaki je zan biki. Na kwana biyu ban je ba" na kalli Daddy sannan na kalle shi nace "Okay" na juya na fita a raina ina fatan sanda zan tafi ya manta ko kuma baya gidan, amma sai dai ina fitowa na ganshi a zaune a rumfar motoci yana danna waya, ina shiga mota kuwa yazo ya shiga ya zauna a passengers seat, naji kamar zan saka kuka amma a haka na kunna motar muka fita. Muna fita guards dina suka biyo bayan mu. Ya juya ya kalle su yace "seriously! I am here, what more protection do you want?" Nace "maybe protection from you" yayi dariya, "you are kidding right? In zan miki wani abu baa hanya zanyi miki ba" nayi shiru na rabu da shi dan na san dama neman magana ne ya saka shi biyo ni, ni kuma yanzu magana ita ce abinda bana son yi shi yasa nake barin gidan. Muka cigaba da tafiya sai yace "Ban gaya wa Mommy ko Daddy ba" ban kalle shi ba nace "what?" Yace'"maganar mijin Safina" nayi shiru na rabu da shi, ya cigaba"baki tambaye ni dalilin da yasa ban gaya musu ba" still bance komai ba, sai yace "dalilin da yasa ban gaya musu ba shine exactly dalilin da yasa ban gaya wa Daddy inda kika je ranar nan ba" nace "and what reason was that?" Yace "because I care. I care about you and I want you to trust me. Ina so ki fahimci cewa I am loyal to you.And I am very trustworthy" nayi ajjiyar zuciya nace "wai dan Allah Mustapha kai baka da budurwa ne da zaka je ka dama? Kai ko zancen nan ma ba ka zuwa? At & least go out and meet people, maybe zaka samu mai sonka one day" yace "yammata akwai su mana, su da kansu suke kawo kansu, but the problem is I already have my eyes and heart somewhere. I just want to be seen. I just want my efforts to be appreciated". Sai da muka je nayi packing sannan na juyo ina kalion sa nace "Mustapha, it is not going to happen. Let it go. Don't drag please, we have been through this before. Ka bar maganar dan Allah" na bude kofar zan fita sai ya kira sunana, na juyo ina kallon sa sai yace "and neither will you and Muhammad happen. Daddy ba zai taba bari ki auri mijin Safina ba". Na fita daga motar da sauri na shiga dakin da nake zama a ciki duk sanda na je gidan na rufe kofa sannan na jingina da jikin kofar. Ba maganar sa ce ta bata min rai ba abinda ya bata min shine the fact that he is right. Daddy will never let it happen. Idan da ace Daddy zai samu yadda yake so to zai so in auri wanda yake kusa da ni, someone like Mustapha, someone da ba za'a yi bincike ba idan zaa5yi auren. lyayen Muhammad ma ba zasu barshi ya aure ni ba considering alaka ta da Safina, ko zasu bari ma zasu yi bincike, and chances are high that they will find out about my fast, I am sure Safina zata basu labari ko da basu tambaye ta ba, And as righteous as they are, they will never let him marry someone da take da dan shege. So Mustapha is right. It is never going to happen. And just as if to rub salt on my wound sai ga kira nan ya shigo waya ta from an unknown number, a take na san cewa shine, and my stupid heart pick up the call na saka a kunne na, ya sake yin shiru irin na jiya, nima kuma nayi shirun, sai daga baya ya kira ni da sunana shi kadai yake kira na da shi "Piya" na ji hawaye naya bin fuska ta amma ban amsa ba, ya cigaba "I know you can hear me, please ki bani ko da minti biyu ne inyi miki magana, I just want you to listen to me" and I listened to him as he try to pour his heart out to me, sai da naji kuka yana kokarin kwace min sannan na katse kiran without saying a word to him. Sannan nayi blocking number din ita ma. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya mana, kullum sai Muhammad ya saka sabuwar number ya kira ni, farko ina dauka ba dan komai ba sai dan inji muryarsa in samu sanyi a zuciya ta, daga baya sai na daina dauka dan na fahimci sauraron nasa was doing more harm to my heart than good, Giving me false hope, Da ya ga na daina dauka sai ya koma turo min messages, kamar dosage na magani haka ya riga feeding dina da soyayyar sa, safe, rana, dare, har zama nake yi in saka waya ta a gaba ina jiran shigowar sakon sa. And when the nights get lonely sai in zauna inyi ta bitar messages dinsa kamar mai dorin karatu. A haka har muka tafi Umrah nibda Hajiya, naji dadin tafiyar tamu sosai musamman peace din da na samu a zuciyata sanda na taka kafa ta a cikin garin Madina, and the weight da naji any lifting daga zuciyata sanda nayi kuka a cikin sujjada ta a gaban ka'aba. A ranar ne bayan mun koma masauki Hajiya ta saka ni a gaba da tambaya. "Kina da wani problem ne Safiyya? Akwai abinda yake damun ki?" Na girgiza kaina da sauri laughing nervously, "bani da wani problem Hajiya, me kika gani?" Tace "dazu kukan da kika yi a gaban ka'aba is not normal. Abu biyu zai saka mutum wannan kukan, ko dai wani babban zunubi da kayi nadama akan sa kake neman gafarar ubangiji ko kuma wani problem da kake da shi kake neman Allah ya baka mafita" nayi shiru ina niyyar ce mata bani da problem amma sai hawaye na yayi betraying dina, Ta zauna tana kallo na kawai, sai kuma tace "kin san yanzu da nake kallon ki me kika tuna min dashi?" Na goge hawaye na tare da girgiza kaina, sai tace "mahaifiyar ki. Ganin da na fara yi mata a duniya. Ranar da Hajiya Kyauta ta kawo min ita gida na. I have never seen anyone as broken as she was, she was so sad. But you know what? She was also determined. She had a purpose. Aim dinta a lokacin shine tayi all that she can a rayuwa so that zuri'ar ta, ma'ana you, will not be in her situation. Bata da komai kuma bata iya komai ba a lokacin, hatta shara sai da aka koya mata dan bata ¡ya irin ta mu ba. But she worked hard, harder than anyone I have known. She took risks, risks that even I couldn't. And all for you. At the end kuma, she gave her life for yours". Nayi shiru ina jin ta, wondering if her words are to make me feel better or worst. Sai ta cigaba "but yanzu da nake ganin ki a wannan halin sai na samu kaina da tambayar kaina, All that your mother did are for what? Because you are as broken and devastated as she was lokacin da ta shigo Abuja. To hakan yana nufin all her sacrifices have been in vain kenan?" Na girgiza kaina "Ammie was mistaken. Money doesn't buy happiness. It only creates problem. Well at least it did for me. Gani da kudin dai yanzu but ba zan ¡ya siyan abinda zai saka ni farin ciki ba" Hajiya ta girgiza kanta "no Safiyya. You are mistaken not her. Money doesn't buy all happiness, yes, amma talauci ma haka. Money can create problems tabbas, amma talauci ya fi shi creating problems. Kowa da kaddarar sa, whether you are talaka ko mai kudi. Safiyya, happiness can only be found from within, you are the only one responsible for your happiness not abinda kike da shi and not mutanen da kike tare da su. Only you and the choices you make can make you happy" Two weeks muka yi a can muka dawo Nigeria, and sanda muka dawo I felt a lot better duk da dai har lokacin ban samu solution to MG problem ba. Sai dai kuma a ranar da muka dawo din muna zaune a falo da kowa da kowa har da twins sai ga waya anyi wa Mommy, tace Safina ce ta kira ta "maybe zata ce zata zo miki sannu da zuwa ne" ta fada sannan ta dauki kiran, amma kuma tana dauka sai muka ga ta mike tsaye cikin tashin hankali "accident? Wanne irin accident? Ban gane ba, Safina ce tayi accident ko mijinta? Tare suka yi? Ni fa ban gane ba, suna ina?" Na mike tsaye ina kallon ta ido na kamar zai fado kasa. Ta bi mu da kallo, jikinta har rawa yake yi "'Ramla ce, yarinyar da na kaiwa Safina, wai mijin Safina ne yayi accident. Ita ma kuma Safinan wai tayi accident. Ni ban gane ba. Kuma tace ba tare suka yi ba". Na juya da gudu nayi waje, sai da na kama handle din mota ta sannan na tuna ban dauko key ba, na koma gurin daya motar da bata bukatar key na bude ta da fingerprint dina hannuna yana karkarwa sannan na shiga na tashe ta na fita daga gidan a guje. Him👳🏻‍♀️ It has been 3 weeks already yana ta bin Safiyya amma ya kasa samun ko da response ne from her, ya zama as frustrated as anyone can be. Ya zama kuma very irritable, abu kadan ne yake bata masa rai, Punching bag dinsa kuwa tana shan duka dai dai gwargwado, And he tried as much as he can to avoid Safina dan yana gain zai iya rufe ta da duka anytime dan koda yaushe zuciyar sa tuna masa take yi cewa Safina ce sila, duk halin da yake ciki a yanzu ita ce ta ja masa. And then ranar nan, ya dawo daga office a gajiye ga yunwada yake ji, ya taho da takeaway din abinci, ya shiga falonsa ya zauna akan dinning table ya bude abincin ya fara ci kenan ta shigo. Ya rufe idonsa yana karanto adduoin samun nutsuwa, ta karaso inda yake ta ja kujera ta zauna tana facing dinsa, ya cigaba da cin abincin pretending as if bai san tana gurin ba. Tace "sannu da zuwa" ya cigaba da cin abincin sa, sai ta kalli abincin tace "I have cooked for you you know? You don't have to buy food outside" ya dago ido yana kallon ta, sai kuma ya girgiza kansa ya cigaba da cin abincin sa, tace "it is still not too late Muhammad, we can start all this over again. Idan da zaka manta da abinda baka da shi kayi concentrating akan abinda kake da shi, then we can be happy. Dole mu samu a way out of this life kafin babyn nan yazo Muhammad, we cannot bring him into this world a cikin wannan yanayin" ta fada tana shafa cikin ta, "he is your blood and he is innocent" ya ajiye cokalin hannunsa yace "you made the decision to bring him into this world at this time Safina not me, dan haka laifin ki ne ba nawa ba. Take the fault for once". Ta girgiza kanta, "how can you say that? Da ma akwai wanda yake making decision sanda za'a haifi wani idan ba Allah ba. Kar kiyayya ta saka ka yin sabo dai" yace "you know what I mean, and as always kina kokarin kiyi twisting maganar ne. And since we are talking about this, I want to know me kika yi min a ranar nan" ta girgiza kanta "ni ban yi maka komai ba" yace "karya kike yi. Ke ma kuma kin san karya kike yi. Asiri kika yi min ko? Shirka kika aikata kawai dan ki kaini kan gadon ki ko? Was that it?" Ta fara hawaye "ni wallahi ba asiri nayi maka ba. Ta yaya ma zaka yi kace haka? Ka san abinda ya faru ai, I went to your room nayi wanka and bayan na dawo daki na you came da kanka" yace "yanzu duk toilet din da suke gidan nan ki rasa a wanne zaki yi wanka cikin dare sai na bedroom dina? Just because kin san abinda kika yi and you wanted to like add more salt to the wound ko?" Ya mike tsaye cikin fada, ya nuna ta "you are going to tell me what you did on way or another because idan har asiri kika yi dole ki bar gidan nan da ba zan cigaba da zama na mashirikiya ba, you are going to explain it to Mama, a lokacin zata san who you really are" ta mike ita ma "ni ban yi maka asiri ba, me yasa wai duk wani worst abu kake danganta shi da nine? I just wanted my husband to love me, I thought you would love me" ya matsa kusa da ita yace "and you did what?" Ta juya tana kallon kettle dinsa da take jone a socket. Ya kalla shima, sannan ya kalle ta, "a ciki kika saka asirin?" Tace "ba asiri bane ba na gaya maka" yace "menene to?" Ta sunkuyar da kanta kasa tace "desire pill". Ya bude baki cikin mamaki sannan ya fara ja da baya "desire pill?" Ya maimaita "'yanzu lalacewar ki har ta kai haka dama Safina? Yanzu abinda na dauko na kawo gida na kenan?" Ta fara kokarin kare kanta '"I tried everything I could to get your attention Muhammad, har abinda ban taba tunanin zanyi ba a rayuwata nayi saboda kai, na kaskantar da kaina iya kar kaskantarwa. I thought...." Sai kuma ta kasa karasa maganar saboda wani mugun kallo da yake yi mata. Ya sake taku biyu zuwa gare ta yace "yanzu ke har kinsan kiyi wa namiji amfani da irin wannan abun dan ya kwanta da ke? Maza nawa kika saka wa? Huh? Nawa? Now am not even sure if that is mine" ya fada yana nuna cikin ta. Fuskarta ta nuna bacin rai tace "me kake nufi? You are crossing a line kuma Muhammad . Kai ne babban shaida ta cewa kai ne namiji na farko a gare ni. Kuma kai ne na karshe. Then how can you accuse me of that?" Yace "nine shaida? I am not sure of abinda na tarar ai. Since kinyi wayewar using desire pill am sure kinyi wayewar faking abinda kike magana akai. I read cewa yammata suna iya Watsewar su a waje su yi na fake su kai gidan miji kuma. And I am sure you can do that. So wannan dan in kin haife shi sai anyi masa dna sannan zan karbe shi". Ta zame ta zauna akan kujera tana dafe kirjinta, daga dukkan alama bai taba gaya mata mai zafin ta yau ba. Tayi shiru ta kasa magana tana kallonsa, sannan a hankali tace "i have been good. I kept my chastity and brought my virginity to my married home na kuma bawa mijina na sunna, Ni ba yar iska bace ba Muhammad. Yan iska suna can a inda suke. Amma ni kake yiwa kazafin zina sannan kake sheganta min dan da na samu cikin sa a dakin auren sunna, dakin auren ka. Bayan shegun suna can a inda suke." Yace "I am not sure about that, sai kin haihu naji abinda likita yace" tace "na yarda za'a yi dna din, just dan kar ayi wa dana tambarin da aka yi wa nata. Just dan kar ayi min tambarin da aka yi mata" ya juyo yana kallon ta, ita ma shi take kalla cikin ido, babu sauran toro a idonta, kukan ma ya tsaya. Yaji zuciyar sa tayi contracting yace "ita wa kenan?" Ta mike tsaye tana kallon cikin idonsa tace "kasan wadda nake nufi ai" ya karaso ya tsaya a gabanta cikin kaurin murya yace "say her name if you dare" tace "Safiyya. Safiyya Adam Muhammad" yayi shiru yana kare mata kallo, not knowing what to think and she helped him clear his doubts "amsar da kayi ta nema kwanan baya ita ce zan gaya maka yau, cikin da ka gani a jikin Safiyya last year cikin gaskiya ne. Kuma na shege ne. She slept with so many men that she couldn't even name the father of her unborn baby, Sai da ta haifa sannan akayi dna. Wannan ya sa Daddy a kokarin rufe abin kunyar da tayi ya aura mata Mukhtar. Wannan ne dalilin da yasa tayi breaking up with you dan tasan iyayenka ba zasu bari ka auri someone like her ba. A yanzu haka tana da dan shege yana nan a raye hiding somewhere only she knows" Yayi taku biyu baya yana girgiza kansa "you are a liar" tayi murmushi, "not this time, I am not. In baka yarda ba go and look into her eyes and ask her idan bata yi cikin shege ba, go ask her idan bata da dan shege" "You are lying" ya sake fada, idanunsa suna juyewa, yana jin jiri yana neman daukan sa, yes abinda ta fada na ciki made sense, it answered a lot of questions. Amma zuciyar sa ba zata iya daukan gaskiyar ba. Ji yake yi kamar zata bar kirjinsa. Da baya yake tafiya har ya bar dining din ya shiga falon sa, wani jiri ya debe shi ya fadi akan kujera a falon ya dafe kansa, ta karaso inda yake da sauri already tana regretting abinda ta gaya masa, ta rike shi "Muhammad!" Ya mike tsaye da sauri sannan ya sauke maruka guda uku akan fuskarta, saboda karfin marin sai da ta kai har kasa, ya wuce ta da sauri ya dauki key din motarsa ya fice daga falon da sauri. Ta hango fitarsa, abinda ta fara tunani shine mota zai shiga, ta mike da sauri duk kuwa da dishi dishin da take gani amma ta bishi, ta san shi da gudu a mota a halin lafiya lau ma ballantana a halin da yake ciki. Ta fita a daidai lokacin da yake yiwa mota key, ta karasa da sauri "Muhammad. Dan Allah ka tsaya, kar kayi driving, dan Allah ka tsaya, tayi kokarin rike motar yayin da shi kuma ba tare da ya lura da fitowar ta ba ballantana yaga ta rike mota ya ja motar a guje, motar ta ja ta da karfi sannan ta fadi a kan cikin ta a tsakiyar compound din gidan a daidai lokacin da Ramla ta fito saboda jin muryarta da tayi tana magana da karfi. A guje ya fitar da motar da ga gidan, wannan ya sa bai kalli titin ba ya hau kai a guje, motar da ta taho a guje akan titin itama ta daki side din tasa motar, nan take motar ta sa ta fara adungure a kan titin, sai da ta dungura sau uku sannan ta tsaya, Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA❤️‍🩹 Episode Fifty Two: Together Naji wata irin faduwar gaba, "what?" Na tambaye shi a tsorace, sannan na juya ina kallon layin mu da muka fito da ga ciki "Muhammad what are you doing. This will make things worse, wannan ba zai gyara komai ba sai dai ya kara batawa. Dan Allah ka tsaya. Dan Allah ka tsaya muyi magana you will understand abinda nake nufi". Bai ko juyo ya kalle ni ba ya cigaba da driving dinsa, na sake kokarin yi masa magana "to ina zaka kaini ma wai? Ina zamuje?" Bai kalle ni ba yace "I don't know. But we will figure it out" na girgiza kaina "I understand ranka ne a bace, annabi ma ya hana yanke hukunci a cikin bacin rai. Please park the car and let's calm down a bit, we will figure things out", Bai amsa min ba sai ma kara gudun motar da yayi yana ta wuce motoci, wannan ya kara tabbatar min da bacin ran da yake ciki, in dai yana irin wannan driving din to either ransa a bace yake ko kuma he is stressed or tired, amma idan yana cikin farin ciki musamman in muna hira mai dad a mota to a hankali yake driving, most of the times ma dead slow yake tafiya. Na juya kaina ina kalion motocin da muke wucewa toro yana kamani, what if wani abun ya same mu kuma? Na waiga baya na and I saw my guards following us and I calmed down a bit, at least someone is on the look out for us. Na sake juyowa ina kallon sa, trying to get him to look at me "Muhammad dan Allah slow down. Please park the car. Let me drive, I will take us to duk inda kake son muje" ya dan kalle ni kadan sannan ya sake mayar da idonsa kan driving dinsa, na sake cewa "Please Yay Muhammad". Ya sha wata kwanar da ta hau da mu kan babban titi, shan kwanar da yayi a guje ya saka naji faduwar wani abu a seat din baya, na juya and I saw yar karamar jakar takardun sa, I have seen it ones and he told me it contains all the important documents na rayuwar sa. Na juya da sauri na dauko ta na bude, making sure ita din ce, sannan na rufe ina kallon sa idona cike da hawaye, wato da gaske yake kenan, Ya kalle ni shima sannan ya kaill jakar hannuna yace "We will need them, Dole zan bukaci neman aiki so that I can take care of you" naji hawayen sun karasa gangaro wa, poor Muhammad, neman aiki yake so yayi dan ya samu kudin da zai kula da ni, ni Safiyya. How innocent of him, Ya cigaba da magana. "I have some little money in my account. We can get you some clothes with it. And we can also get a place to stay for a while. And other necessities, Then I will look for a job. Or get some business started. Ke kuma sai ki koma school. Not MD though. We are going to be Okay. Like you said, everything is going to be alright". Na goge hawaye na sannan na rufe jakar na ajiye ta a gabana. Abinda na fahimta a lokacin shine the only way to get to him shine in nuna masa na yarda da abinda yake lissafawa, that will calmed him down. In naki he will only get more angry. Nace "I can work nima. I can get a job da baya bukatar takardun makaranta. Na iya girki, zan iya samun aiki a restaurant or something" ya girgiza kai "no, you will not work in a restaurant, Sai dai kiyi a gida. Irin wanda ake yi ana order din nan, I can do the delivery" nayi murmushi tare da kwantar da kaina a jikin kujera ina kallon sa nace "no. Ba zaka yi delivery ba, Haka kawai in mata sunyi order su ringa ganin ka? We will get a delivery man. Sai a siva masa abin hawa, Bana son yammata suke gane min kaj" and I saw his body relaxed, har rikon da yayi wa wheel din ma karfin sa ya ragu, his eyes softened, ya juyo ya kalle ni yace "ohh, and kuma kika ce zaki yi aiki a restaurant. Kin dauka ni zan barki kina serving maza?" Na bude ido "hey, ba fa waitress nace zan zama ba. Just a coOk, A kitchen zan ke aiki na. Babu ruwana da customers" yace "still. It may get crowded. And yadda kika iya girkin nan someone may say yana son ya ga mai girkin. Gwara kiyi girkin a gida ni kuma inyi delivery" nayi murmushi ina kallon fuskarsa "you will be the cutest delivery guy ever, that's why ba zan barka ba, Sai dai in zaka ke saka nikab" and he laughed. Kar karamar dariya but ta chanja yanayin fuskarsa gabakidaya, ya dan dafe kansa da hannunsa daya yana cigaba da driving da daya hannun, zuwa lokacin ya koma driving slowly. A hankali nace "sannu, Kan ka ne yake ciwo? Let me drive" ya girgiza kansa "I am fine" nace "ka san dai | am a better driver than you ko? Look at what your rough driving caused you, Kaje ka fasa kai ka kusa ka jawo min asara" na fada ina nuna bandage din kan sa, ya dan taba gurin ciwon tare da bata fuska alamar vana vi masa zafi sai kuma yace "shi yasa in muka haihu ke zaki ke driving yara zuwa school, dan in suna yi min hayaniya a mota za'a iya samun matsala" nace "to in ka bani motar da wacce zaka ke zuwa office?" Yace "kafin nan na sayi wata ai. It won't take me long to find a job. But ban san yadda zaki ringa hada makaranta da catering services da kuma school runs din yara ba. Sai dai a samo musu driver" nace "another car kenan fa. Ga kuma kudin salary din driver. Dole sai mun koyi managing abubuwa fa" ya juyo yana kallona da dariya a muryarsa yace "who are you? Where is Safiyya Adam Muhammad, the girl that always want to spend money and buy classy things and enjoy soft life. Ke ce kike zancen a tattala kudi kuma yanzu?" Nayi murmushi "to yaya zanyi? Yana yin rayuwa ne ya chanja. Dara kudin Daddy nake kashewa yanzu kuma any kidnapping dina daga gidan Daddy and I am on a run. Zuwa inda not even my kidnapper knows. Dole yanayin tunani na ya chanja zuwa survival instinct". Muka danyi shiru babu wanda yake magana for a while muna cigaba da tafiya a titin barin gari kowa yana lissafi a cikin zuciyarsa. Waya ta tayi kara, na duba naga number din one of my body guards ne, na dauka na saka a kunne na sai va tambaye ni if I am okay, a hankali nace "I am fine" sannan na katse kiran. Ya miko min hannun sa yayi min alamar in bashi waya ta, nayi ajjiyar zuciya na mika masa sai ya kashe ta ya ajiye a tsakanin mu sannan ya dauko ta sa ita ma ya kashe ya ajiye. Muka cigaba da tafiya sai kuma yace "You will continue to have the kind of life you are used to, or even more. I will work hard kinji" nayi shiru ina kallon sa, imagining the kind of life da muka gama shiryawa yanzu a cikin motar nan, just me and him alone in the world. Sai kuma nace "It would have been a good life. A great life in dai da akwai ka a ciki. But it is just a dream Muhammad. We cannot have that in reality. We have responsibilities, Responsibilities to our parents. They love us, they love us more than anything. They do not deserve this from us" ya kalle ni yace "and do you think we deserve what we are going through? Wanne laifin muka aikata?" Nace "ba muyi laifin korai ba, amma basu sani ba ai. We just need to get them to listen to us and to understand us, na tabbatar ba zasu yanke mana hukuncin da zai cutar da mu ba. Saboda sun fi mu san kan mu" yace "aha! And that is exactly what I am trying to do. To get them to understand. To understand that I cannot continue living like this. I cannot continue living without you". Na sake cewa "not like this Muhammad. This will break their hearts. Zasu ga kamar mun zabi junan mu ne a maimakon su. Ba zasu ji dadin hakan ba. Muma ba zamu ji dadin hakan ba. We need to do this the right way". Ya juya motar zuwa gefen titi yayi packing dinta sannan ya juyo yana kallona yace "then tell me which way is the right way. I tried explaining things to Mama ta kasa fahimta kuma banga laifin ta ba saboda nima ban fahimta ba. All you have been telling me in this relationship is nothing. Sometimes it felt as if I am in this relationship alone. Baki gaya min komai ba ban san komai akan ki ba, ban gane komai ba ta yaya zan fahimtar da su? All I know shine ina son ki and I know you love me bayan hakan ban san komai ba. Then ran daya you just appeared like that and told me Wai Kina da aure gashi har Kina halin damuwar da yake ciki a yanzu ni na jefa shi a ciki. A hankali nace "I am sorry Muhammad" ya nuna ni "if you say you are sorry one more time....." . " Sal kuma ya mayar da hannun ya ajiye yana kallo na, trying to calm himself down. Sannan kuma murya can kasa yace "you have no idea how stubborn your love have been a cikin zuciyata, You have no idea how crazy it almost drove me" ya kalli kansa, with bandages on different parts of his body yace "hell, I am not sure ma ko yayi succeeding in making me crazy. Just look at me. I mean I am literally on a run from my parents after kidnapping you" ya karasa maganar yana dariya, nima dariyar na taya shi, sai kuma yace "I have tried in ga na cire ki daga raina Safiyya Adam na kasa, I mean you get stuck in my head har zama nake yi muyi hira a cikin kaina wani lokacin muyi fada in baki hakuri ko da ba nine da laifi ba". Na rufe fuskata da hannuna ina dariya sannan na bude nace "dole a bani hakuri in ba haka ba asha rigima" ya girgiza kai "piya, you are impossible" muka danyi shiru, zuwa lokacin gari yayi duhu sosai, sai kuma on a more serious note nace masa "na san I have not been a good girlfriend to you, Babu abinda na kawo rayuwar ka sai tarin damuwa da emotional torture. Shi ya sa kullum nake baka hakuri, dan bani da abinda zan baka sai hakurin. I mean har a cikin baccina nake baka hakuri...." Ya katse ni "no, kina da wani abu da zaki bani bayan hakuri. Zaki fada min gaskiya, and when I say gaskiya I mean the entire truth. I want to know everything." na gyada kai na "na yarda, You deserve the truth kuma zan gaya maka truth din, gabakidayan ta, Na kuma tabbatar zaka fahimce ni in sha Allah. But Please Muhammad we need to go back home. Na san by now an fara neman mu, musamman kai da kake asibiti, Mama da Abba ba zasu ji dadi ba. And Daddy, ba zan iya yi wa Daddy haka ba Muhammad, ya gaya min kaje ka gan shi ranar nan na tabbatar ka ga yanayin jikin sa, in na tafi na bi saurayi na barshi bakin ciki na will kill him, we will figure this thing out while still under our parents' Yayi ajjiyar zuciya "you are right. I was wrong to try taking you away from Daddy. Zan mayar da ke gida. But I also want you to promise me two things. Na farko zaki gaya min gaskiya akan komai ba komai. Na biyu, from now own, no more hiding things from each other, we will do everything together. We will solve the issue with our parents together. We will overcome all the obstacles together", Na gyada kai "na amince, nayi alkawar'" yace "Okay, then start talking ..... From the beginning" Na danyi shiru ina kalion yatsun hannu na sannan nace "it is a long story musamman tunda ina so in fara maka tun daga farko, zan gaya maka kamar yadda nayi alkawari amma ba yanzu ba. We do not have time a yanzu, You need to get back to the hospital. I need to go back home tun kafin hankalin Daddy ya tashi" ya gyara zama yace "we have the whole day..." Daga nesa muka ji ana kiran sallah a wani masallaci. Yayi shiru yana kallona sai nace masa "wannan sallar isha ce ba magrib ba" yayi sauri ya duba agogon motar and the time was 7:52pm. Na sake maimaita masa "We need to get you back to the hospital, and I need to get back home" ya tayar da motar tare da cewa "it is a long way ai. You can tell me in the way", Muka juya mota muka koma daya hannun muka dauki hanyar komawa cikin gari, amu jima muna tafiya ba yayi packing a gaban wani masallaci ya shiga yayi sallah nima nayi alwala na dauko sallaya a cikin motarsa nayi sallah, na lura da motar guards dina a dan nesa da mu kadan. Ina idarwa ya dawo ya sake tayar da motar muka cigaba da tafiya, muna fara tafiyar ya kalle ni yace "uhun. Ina jin ki. Start talking" na danyi shiru ina kallon sa, thinking of where to start from. Na san yana bukatar ya fahimci komai, tun daga dalilin da yasa na kasa kai shi gidan mu a wancan lokacin zuwa uzurin Daddy na hana yi min samari wanda shine dalilin da yasa ban kai shi gurin sa din ba, amma ba zai fahimci duk wannan ba sai ya san labarin Ammie. Dan haka daga labarin Ammie ya kamata in fara yi masa, ko kuma ma ince daga labarin Baba Hadiza. Na dauki waya ta na bude pictures nayi scrolling zuwa hoton su Ammie da na dauka ranar nan a waya ta, na nuna masa tare da nuna Ammie nace "wannan ita ce mahaifiyata" ya kalle ta sannan ya kalle ni, "kuma kama sosa'" nayi murmushi "Nagode" yace "Allah ya yi mata rahama" nace "Amen" sai kuma na nuna Baba Hadiza nace "wannan mahaifiyar ta ce, sunan ta Baba Hadiza, wadannan kuma yan'uwan ta ne, uwa daya uba daya" ya gyada kai cikin fahimta tate da mayar da hankalinsa kan driving din da yake sai nace "duk sun mutu gabakidaya" yayl sauri ya kalle ni da mamaki "what? Ga baki dayan sup" Na gyada kai "yes, Ammie ce kadal ta girma a cikin su, ita ce ta karshen mutuwa" yace "how? Accident ko menene?" Nace "no they died in different kind of tragedies" na danyi murmushi nace "| used to say that tragedy is another name for my family. Yanzu kuma zan fahimtar da kai dalili", Daga nan sal na bashi labari, labarin Baba Hadiza da iyayenta da yan'uwan ta da yanayin rayuwar su, sai kuma na bashi labarin auren ta da Alhaji Haladu da yanayin zamanta da abokan zamanta har zuwa mutuwar Alhaji Haladu da kuma yadda rayuwa da kasance musu bayan nan. Sannan one by one na bashi labarin yadda suka mutu, tun daga kan Khadijah har zuwa kan Sauda, da kuma yadda Ammie ta gudu dan kar ayi mata irin auren Baba Hadiza, dan kar ta haife ni in rayu cikin wahala kamar yadda su suka yi, na bashi labarin shigowar ta Abuja da zamanta a gidan Hajiya. Duk a cikin labarin nawa in dai aka zo kan abinda bai fahimta ba zai tambaye ni in sake fahimtar da shi, amma sai na ga labarin Hajiya ya dauki hankalin sa sosai. "you mean Hajiya Maryama? Yayar Mommy?" Na gyada kai "eh ita. I guess you already know her" yace "naje gidan ta ones, she said ta san grandma dina, and ranar nan ita ma grandma take ce min ta san ta and she said she knows her daughter mai suna Safiya, wai kuma ta auri wani mai suna Adam. I told her bata da yaya amma she insisted tana da ya mai suna Safiya" nayi murmushi ina jin dadi, nace "haka take cewa, cewa take yi yarta ce, amma in reality yar aikin ta ce. And she was so kind to her in ways that I cannot describe" muka sake yin shiru a lokacin da muke shigowa unguwar mu. Ya je yayi packing a kofar gidan mu yana kallona yace "yanzu cewa zaki yi zaki shiga gida ki bar ni ko?" Nace "ko zaka zo mu shiga tare?" Ya kama handle din kofa "finally za*a kai ni wajen Daddy" nayi dariya "rufa min asiri. Wasa nake maka fa" ya langwabe kai "still da'" nace "ka dan kara min lokaci kadan. I need to prepare him. I need to find words da zanyi using to convince him" ya kalli gate din mu yace "you need the words now" na juya nima na kalla and I saw Malam Ya'u a tsaye yana kallon mu sai kuma ya juya ya koma cikin gidan. Nayi ajjiyar zuciya nace "l really don't know me zan ce masa, amma kaima kana bukatar words din da zaka fada a gida" yayi ajjiyar zuciya "I think we should just tell them the truth, sai muga abinda zasu yi akai. Kamar yadda kika ce, they love us and will make the right decision for us". Na dauki wayata na rike ina juijuya ta ina kallon sa, feeling reluctant, kamar kar in fita daga motar, kamar kar in rabu da shi, but kamar yadda nace, we must face our reality. Sai kuma nace "good night Malam Muhammadu" na bude kofa na fita da sauri sai ya kira sunana "Piya" na juyo ina kallon sa sai yace "don't get married again" nayi murmushi "I will, I will get married. And you will be the groom" sal kuma naji kunyar kalion da yayi min na yi cikin gida da sauri. Amma sai na tsava a jikin gate, ban matsa ba sai da naji alamar ya tafi sannan na yi hanyar cikin gida ina harhada kalamai a raina. A hanya muka hadu da Baba Ya'u yana fitowa daga bangaren Daddy, nace "sannu Baba Ya'u" ya bini da kallo yace "sannu ranki ya dade. An dawo lafiya?" Nace "lafiya lau" sai ya koma gurin zaman sa ni kuma na shiga cikin gidan. Na san dai Mommy tana asibiti wajen Safina, though ban sani ba ko ta dawo gida bayan na fita, Mustapha kuma da twins tunda ban gansu a waje ba kuma basa falo na san maybe sunyi bacci, amma Daddy na san idonsa biyu tunda yanzu naga Baba Ya'u ya fito daga gurin sa. Ma san kuma ya kamata inje in gan shi ya ganni, amma kuma ban san me zan ce masa ba. Kitchen a fara shiga ina neman abinda zanci dan yunwa nake ji, gwara ko fadan za'a yi min ayi min da abinci a ciki na kar a gama yi min fadan kuma in kasa cin abinci. Na samu abinci na zuba, na hada smoothie na na sha sannan na tafi part din Daddy. Yana zaune ya saka tv a gaba amma daga gani kasan ba ita yake kallo ba. Na shiga da sallama "Daddy ba ka kwanta ba?" Ya daga kai ya kalli agogo sannan na juyo yana kallo na fuskarsa cike da damuwa. Na karasa gabansa "barka da dare Daddy" yace "kin dawo? Ya jikin Safinan?" Na sunkuyar da kaina ban ce komai ba ina jiran inji ta inda fadan zai fara sauka kaina, ko kuma at least ya tambaye ni ina naje amma sai naji yayi shiru bai ce komai ba, sai dai fuskar sa a cike take fal da damuwa, Haka na gaji da zama sai nace "Daddy a kashe maka tvn ka je ka kwanta? It is getting very late" yace "ki barshi, Ki je ki kwanta" sat nail ban Il dadi ba, bana son jayi fushi da ni, so hake yayi min tada ya aye min abinda nayi ba dal dal bane ba in yaso ni kuma sat inyi masa bayant Amma kuma ko bayanin ne ina bukatar hada kalmomin da zanyi bayanin da su. Dan haka wannan fushin da yayi duk da dal banji dadin sa ba amma ya bani chance din shirya case dina, Amma eluk da haka sal nace "Daddy kayl hakur'" bal amsa min ba daga farko sal daga baya yace "akwal abinda kike so kl gaya min ne? Akwai laifi da kike so kiyi confessing?* Na bude baki sal na mayar na rufe ban ce komal ba, sal yace "tashi kI je ki kwanta" har na tashi zan Ata /lkl a sanyaye sai ya kira sunana, na juyo sal yace "abinda ya faru a da ba zai maimaita kansa ba. Do you understand me?" Na gyada kai da sauri *yes, Daddy" na fita da sauri, Daki na na wuce da sauri ina /in babu dad a raina, Na san dal Baba Ya'u abinda zal ce masa shine mjin Safina yazo ya dauke ni a mota, Sannan kuma yanzu zai ce masa mijin Safina ne ya dawo da ni a mota, And I thought he will confront me about menene alaka ta da mijin Safina da har zai bar asibiti ya taho wajena? Kuma ina muka je, But he didn't. And only God knows why. Ina shiga daki na zauna a favorite spot dina, kan gado na ina facing my mother's picture. A raina ina ta saka da warwara ina so in samo hanyar da zanbi wajen warware wanna lamarin ba tare da ran iyayen mu ya baci ba. Kamar yadda Muhammad ya fada, we will have to make them understand, Yes, da mun gudu din da gaske they may understand but in a hard way, ni kuma so nake mu samu mafita ba tare da ran su ya baci ba. Ban samu kwanciya ba sai after two na dare, and still without a concrete solution. Sai dai ina kwanciya waya ta tayi kara na duba naga number din Muhammad, nayi murmushi, duk damuwa ta tana gushe wa, na dauka nace "hey Baby" yace "hey, bulala nawa aka yi miki?" Nace "ko daya. Kai fa?" Yace "they are giving me a silent treatment. Ko fadan ma ba'a yi min ba. Mama da Abba sun gane gurin ki na taho, but the rest are thinking cewa ba'a cikin hayyacina na fita ba. Maybe su maman sun reserving fadan ne for later, " nace "to ko dai meeting suka yi tare da Daddy sanda bama nan? Shima kamar reserving yake yi for later". but the rest are thinking cewa ba'a cikin hayyacina na fita ba, Maybe su maman sun reserving fadan ne for later. " nace "to ko dai meeting suka yi tare da Daddy sanda bama nan? Shima kamar reserving yake yi for later". Yayi dariya, na fahimci he is feeling much better than sanda ya bar asibitin and naji dadin hakan sosai. Yace "I guess we will find out soon enough, Ni dai na san cewa wannan battle din bamu fara shi dan mu daina ba. Yanzu problems a side, yaushe zaki cigaba da bani labarin? I need to know all the details kafin in ja damarar yakin" nace "as soon as any discharging din ka from the hospital. For you to fully understand the next part of the story, ina bukatar in nuna maka wani abu" yace "Okay. Tomorrow zasu sallame ni insha Allah. Highest next tomorrow" nace "Okay, baka da lafiya, bara in barka ka samu bacci sosai, good night" yace "good night, and don't forget to dream about me". And I did dreamt of him, Muna ta hira muna dariya, And it was the best dream da na vi a cikin shekaru. Him👳🏻‍♀️ Sai da ya tabbatar ta shiga gida sannan ya tayar da motar yana murmushi, ya tuno kalaman ta na karshe sai ya girgiza kansa cikin jin dadi, sai kuma yayi sauri ya dafe kan "ouch!" Ya fada vana jin zafin ciwon da yake kan nasa, shi da har ya manta da shi, lokacin da suke tare kamar ciwon ya warke, kamar ma bai ji ciwon ba, yanzu kuwa sai yaji ciwon ya dawo. Maybe dama ita ce maganin, Ya fara tunanin abinda yake gabansa, yadda zai fuskaci iyayensa dan ya tabbatar zuwa yanzu sun san me yayi, gashi ya kashe wayarsa dan haka sun yi ta neman sa a waya ma basu same shi ba. Ya yarda Safiyya ta fi shi gaskiya, their parents do not deserve this. But he just love her a lot. Yayi tunanin zuwa gida saboda ya san by now sun bar asibitin sun koma gida amma kuma cion da kansa yake yi masa ya saka ya chanja shawara ya juya zuwa hanyar asibiti, ga shoulder dinsa ma sai yanzu ya tuna da ciwo a wajen, and maybe driving din da yayi ne ya saka take masa zugin azabar zafi. Kafin ya karasa asibitin ya hada gumi, yana zuwa yayi packing sannan ya shiga reception, yana shiga Wata nurse ta ganshi ta ce "ga patient din da ake nema ya dawo". Ya karasa kan kanta yace da attending nurse *just give me something for the pain* sal wani doctor yazo ya kama shi yace "let me take you to your room, and then we will see what we will do about the pain", Aka mayar da shi dakin da va gudu daga ciki aka kwantar da shi a kan dawo sannan aka mayar masa da drip din da ya cire, ya kwanta ya rufe idonsa yana jin likitocin suna ta zirga zirga a kan sa, a hakan ya fahimci cewa su Mama sunyi ta neman sa anan asibitin sai suka yi waya gida aka ce musu yaje can shine suka tafi neman sa can din, maybe har gidajen yan'uwa an zagaya neman sa. Ai kam sanda suka zo kungiya guda suka Zo, with all his uncles and aunties, yana jin mamie tana maganar zata nemi asibitin suyi referring dinsa zuwa asibitin ta, she is a neurosurgeon kuma wai suna tunanin buguwar da yay aka ce ta saka shi ya fita ba tare da ya san ya fita din ba. Kowa sai lallaba shi yake yi, tun daga kan ma'aikatan asibitin har zuwa kan family dinsa, a cikin yan duba shin yaji har da muryar Mommyn Safina, amma sai ya cigaba de pretending kamar bace/ yake yI har sai da ta fita, amma daya bude Ido ya kalli Mama sa yasan cewa ta san yana sane ya fita, kuma tasan inda yaje. And she looks very disappointed in him, Sal dai bata ce masa komai ba. Ranar Abba ne da kansa yace zai kwana a gurinsa a asibiti instead of Haidar da yake kwana da, Sai bayan da kowa ya tafi Abba kuma yayi alwala ya tayar da sallah sannan Muhammad ya mike ya dauki wayarsa ya cire drip din hannunsa ya shiga toilet kamar zai kama ruwa and he called her. She answered immediately with "hey Baby". And ranar yayi baccin da ya jima bai yi mai dadi irin sa ba. Ba wai problem din ne babu ba, but with her by his side, yasan they can overcome any obstacle together, Maman Maama✍🏻[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Satiyya❤️‍🩹 Episode Fifty Three: A Forever Thing 2 Washegari da safe ma yayl bacel sosal bayan ya koma ya kwanta after subh, Maganganun Mamie da Mama ne suka tashe shi, "Wannan yaron fa babu abinda yake damunsa ina gaya miki Moon, ki rabu da shi kawal, tsabar rashin Jin magana ne a cikin kansa ba elwo ba" Mamie tace "amma ya kamata muy) confirming first kafin muce babu komal, Ni sam bana jin dadin ganin sa a haka wallahi, KI bari in tafi da shi can asibitin koma menene sal mu tabbatar a can" Mama tace "kashi ina baki kina kin karba, Yana sane ta yake komal in gaya miki. Wal yaron nan jlya fa shirin guduwa yayl, har da zuwa gida ya hada kaya akwati guda, har da daukan takardun makaranta ya zuba a mota ya tafi, Kamar irin yammatan nan na da da suke guduwa daga gida su shige duniya idan za'a yi musu auren dole", Mamie ta yara dariya "kal Zainab, gidadon ne zal gudu daga gida, Salihin yaro irin wannan. A cikin yaran mu fa Allah Gidado yana daga cikin nutsatstsun cikin su. To saboda me zai gudu? Mama tayi kwafa yanzu kike cewa nutsatstse, yaron nan fa duk inda kike tunani ya wuce nan. Wai dan nayi masa fada ne fa shine ya je ya hada kaya zai gudu, ko gidan war wa zai je?" Mamie tace "amma akan menene kika yi masa fadan? Let's start from there, nina san ruwa baya tsami banza babana ba mutumin banza bane ba" Mama tace "ai dama bayan sa zaki bi. An kusa a fara lissafa shi a cikin mutanen banzan ai in dai bai chanja halin sa ba. Duk wanda zai bijirewa maganar iyayensa menene shi?" Mamie tace "ni dai ki gaya min Please, akan menene?" Mama tace "to wadannan yaran suna da wani problem ne da ya wuce guda daya?akan wata yarinya ce. Akan wata tsi....." Sai kuma tayi shiru sannan tace "bana son in tsine mata kar ta dawo ta karasa tarwatsa rayuwar yaron nan" sannan sai ta bawa Mamie labarin abunda ta sani game da Safiyya. Duk, maganar da suke yi Muhammad yana jin su, amma sai ya cigaba da pretending kamar bacci yake yi, a ransa yana lissafin cewa wannan ranar is going to be a long day, dan haka bai shirya fara ta yanzu ba. Yana nan kwance har suka gama maganganun su, Mamie ta fahimci point of view din Mama, kuma ta fahimci damuwarta a matsayin ta na uwa, Amma kuma sai ta bata shawara. "Sai mun bi abin a hankali, tunda har yaron nan duk soyayyar da yake yi muku da mu bakidaya ya iya hada kaya zai bar gida to gaskiya sai mun hada da dabara. He loves her deeply. Kuma love either make a person or breaks him. Ya kamata mu bashi listening ear, muji mu kuna saka ido sai mu bashi shawara. Amma kar muyi kokarin forcing din sa in ba haka ba zamu tura shi bango, a karshe kuma zamu iya rasa shi". Mama tace "to wanne irin tura wa zuwa bango ne ya wuce hada kayansa da yayi zai shiga duniya?" Mamie ta sake yin dariya sannan tace "to ba gashi nan ya dawo ba? Yadda ya tafi da kafafuwansa haka ya dawo da kafafuwan sa. So let's start from there. Mu fara tambayar sa dalilin tafiyarsa da kuma dalilin dawowar sa sai muji" Sun jima suna hirar su sannan Mamie tayi wa Mama sallama ta tafi, dama kamar office zata wuce ta biyo. Ya cigaba da kwanciya, duk kuwa da cewa jikinsa ciwo yake yi saboda dadewar da yayi a kwance amma kuma baya son ya tashi yayi facing Mama. Yana nan kwance yaji tace "na san idonka biyu ai. Ka tashi ka ci abinci ka sha magani" Ya tashi zaune yana shafa kai, shi Mama kullum mamaki take bashi akan yadda ba sa iya boye mata komai daga shi har yan'"uwan sa, ko tari suka yi ta san ma'anar sa. Ta bata fuska tace "ta je kayi wanka kayi brush ka zo ka ci abinci" ya mike kamar wani karamin yaro yaje yayi abinda tace ya dawo ya zauna ta zuba masa abinci ta ajiye masa akan table a gaban gadon tace "oya eat". Automatically ya fara saka loma a bakin sa, ita kuma ta zauna opposite dinsa ta zuba masa ido, ya rasa inda zai saka kansa, da kyar abincin yake wucewa. Jira yake yi ta fara magana amma taki farawar har sai da ya cinye abincin da ta zuba tas sannan ta zuba ruwa ta miko masa tare da magani, ya karba ya sha ya mika mata kofin ya cigaba da zama kansa a kasa. Sai kuma tace "tunda har ka iya daukan kafa ka fita kaje gida ka hada kaya ka gudu ai tabbas zaka iya zuwa ka duba matarka da take kwance bata da lafiya k0? Matarka da tayi miscarriage din danka, ko ka manta da ita? Na san maybe ka manta ma kana da aure ko?" Ya dago kai yace "Mama...." Sai kuma yayi shiru saboda wata harara da ta watsa masa, ya sake sunkuyar da kansa, tace "me zaka gaya min ne ni wai? Har kana tunanin zaka zabi budurwa akai na? Akan mu?" Ya girgiza kai "ba haka bane ba Mama. I was just trying to make you understand. To make you listen to me" tace "to I am listening ai yanzu. Fada min? Da ka dauki kayan ina ka tafi? Gidan su kaje ka ce su baka daki? I quess sun hana ka dakin ne shi yasa ka dawo ko?". A hankali yace "gidan su naje, amma ba cewa nayi su bani daki ba. Cewa nayi ta zo mu tafi ........" Sai kuma yayi shiru, ya san maganar ta kara bata ran Mama amma kuma so yake ya gaya mata gaskiyar komai, ta jima sannan tace "ta zo ku tafi ina? Ku shiga duniyar tare?" Yace "nima ban san inda zamu tafi ba. I just took her daga gidan su and we drove out of town. She convinced me to change my mind. Ita ta sa muka dawo. I took her back home ni kuma na dawo nan". Ta danyi shiru sannan tace "in summary, ta fika hankali kenan" ya dago kai ya kalle ta sai kuma ya sake mayar da kansa kasa yace "kiyi hakuri Mama. I am sorry". Ta mike tsaye tayi hanyar waje tana cewa "ka tashi muje ka duba matar ka, ka kuma bata hakurin marinta da kayi, sannan kayi mata jajen barin da tay!" ya mike sannan ya bita a baya. A ransa yana tunanin yadda a cikin laifukan sa bata lissata da ture Safina da mota ba, hakan yana nufin bata yarda ya aikata hakan ba, and wannan realization din ya saka yaji sauki a cikin zuciyarsa. Suka fita daga bangaren da yake suka shiga wanni bangaren daban, sai kuma suka shiga wani daki. Mama ta tura kofar da sallama, Mommy suka tarar a zaune akan kujera tana shan wanj abu a cikin kofi, Safina kuma tana kwance akan gado fuskarta tana kallon daya side din. Mommy da Mama suka gaisa tare da tambayar jikin marasa lafiyan, sai kuma Muhammad ya durkusa ya gaishe da Mommy, ta amsa masa ciki ciki, daga dukkan alama tana fushin abinda take tunanin yayi wa yarta ne. Ya mike tsaye ya tsaya yana kallon Safina da bashi da tabbas din bacci take ko idonta biyu, sai yaga Mama ta fita sannan Mommy ma ta ajiye cup din hannun ta ta bita a baya, Ya zauna a gefen gadon yana kokarin ganin fuskar Safina, sai ya danyi gyaran murya yace "ya jikin?" Ta bude ido tare da juyowa tana kallon sa, He saw yadda idanunta suka fada ciki suka yi ja, sannan kuma side din fuskar ta da ya Mara tayi baki. Daga alama sai marin ya bar mata tabo. Sai yaji babu dadi, ko a mafarki bai taba hango a namiji mai dukan mata ba, ya sake cewa. “ya jikin” ta dauke kai tana kallon gefe tace “as if you care” yace “tunda na tambaya it means I care” tace “mama dai ta saka ka agaba tace kazo kacemin ya jiki. You don’t care ko na mutu ko nayi rai, kawai kana following your mother’s order ne “. Yayi ajiyar zuciya ya mike tsaye yana kallon ta yace you are right, ita tace nazo. But I am truly sorry for that ….’ Yafada yana nuna gurin daya mareta . Ta shafa gurin tace “ I will aware it like a badge of honor, maybe it will serve as a reminder to me, a reminder of how heartless you are” ya tsaya kawai yana kallon ta, aransa yana jin nadamar tausayinta dayaji farkon shigowar sa dakin. Sai ta cigaba “Nasan kayi farin ciki dakaji labarin cewa burinka ya cika the baby is gone. Amma duk kinsa dakayi bazaka chanja wa tuwo suna ba, naka ne” yadaga kafada yace “well, contrary ce what you said, I felt bad da aka gayamin, amma kuma sai na fahimci Allah yana hikimar data saka hakan yakasace, and then, dama ke kika kulla sanadiyyar samuwar sa, yanzu kuma ke kika yi sanadiyyar rashin sa , and I warned you karkiyi kokarin hadani da iyaye na but you didn't listen, yanzun zaki tabbatar cewa sun san abinda zanyi sun kuma san abinda ba zan yi ba". Ya juya zai fita sal ta kira sunansa, har yayi niyyar share ta sai kuma ya tsaya, wata kila a maganganun ta zai samu wani information din da zai kawo masa saukin lamura. Tace "jiya Mommy ta gaya min wai an neme ka ba'a gan ka ba, an aika gida kuma sai mai gadi yace ka zo ka dauki mota a fita, tun a jiyan na gaya wa Mommy cewa gurin Safiyya ka tafi amma taki yarda, har waya ta kira gida aka tabbatar mata da Safiyya bata gida amma bata varda ba. Ni kuma na san can ka je" ya juyo sosai yana kallon ta yace "idan can naje din kuma fa? What will happen?" Tace "nothing. A cikin kwanakin nan, especially yesterday da ka tafi gurin ta, I learnt one of the greatest lessons of my life, that ba zaka taba so na ba, ko ma me zanyi ba zaka so ni ba. Dan haka ba zan sake kokarin komai akan hakan ba. Amma kuma akwai wani abu da na tabbatar shine sakayyar da Allah zaiyi min akan zaluncin da kayi min" tayi shiru tana kallon sa, ya tako ya dawo zuwa gabanta ya tsaya yace "and what is that?" Sai tayi murmushi tace "You will never marry Safiyya. Har abada. Sai dai kuyi ta kallon juna a haka, But you will never be husband and wife" sai shima yayi murmushi yace "and why do you think hakan ne zai faru?" Tace "because our parents will never allow it. Ba ka san halin Daddy ba, ba zai taba aura maka Safiyya ba as long as lam alive. Babban burinsa shine hadin kan gidan sa, ba zai taba bari ka tarwatsa masa gida ba. And your parents too will never allow you to marry kanwar matarka, musamman in suma suka san who she really is and what she did". Ta tsaya suna kallon juna shida ita, tana jiran tajj ya hau masifa or worst. Amma sai taga yayi murmushi. "Tell them please, ki gaya musu. Watakila a lokacin zaki kuma daukan wani darasin, Watakila darasin da zai zama sanadiyyar gyaran rayuwar ki". Ya juya ya fita. Bayan ya koma daki bai jima ba doctor din da yake duba shi yazo yace dama Abba ya nemi a sallame su da safe kafin ya fita, a sake dudduba Muhammad sannan ya rubuta musu sallama, Ya daura shoulder brace a kafadarsa ta hagu inda ya samu dislocation, ya kuma yi warning dinsa against any physical activity da zai saka yayi amfani da yawa da hannun har zuwa nan da two weeks. Suna gamawa Haidar ya zo zai dauke su su tati gida. Mama taje ta gaya wa Mommy sannan bayan ta dawo ta saka Muhammad da Haidar suka je tare suka yi musu sallama sannan duka Zo suka tafi gida, Sai da suka je gida ya samu yayi excusing kansa ya shiga daki sannan ya samu damar kiran Safiyya. "Hey sweetling" "Hey Baby. I have been wanting to call you tun dazu ina toro" ta danyi dariya. Yace "nima. Tun safe ban samu privacy ba sai yanzu. How have you been, Daddy yayi wata magana ne?" Tace "lafiya lau. Just missing you. Ya jikin ka? Hope ba kaje ka sake balla wani kashin ba" yayi dariya "won't do it again ai. Except maybe if I want your attention kuma kin ki bani. Dan na fahimci ciwon nan has been a bliss to me, tun da kinyi fushi da ni yanzu kin sauko" tace "wa yace maka na sauko? 1 just pity you kar ciwon yay maka yawa, but kana warke wa zan cigaba da fushi na" yace "naji na kuma amince. Ni dai in dai za'a bani damar yin rarrashi ko anyi fushin bani da matsala, I know my ways around you" tace "really? What are the ways? Fada min nima in sani" yace "no..... It is my little secret, Ba zan gaya miki ba, Yanzu ma na samu wata sabuwar hanyar, duk sanda kika yi fushi da ni sal in fara rashin lafiya kawal so that you will come running 'Wayyo Yaya Muhammad, i am sorry'™️' ya fada yana kwaikwayon ta, ta fara dariya sai yayi shiru yana sauraron dariyar tata da murmushi kwance akan fuskarsa sannan yace "hey Piya" ta yi shiru tace "yes" yace "I missed you" tace "I missed you too Yaya Muhammad". Sun jima suna hira, sai kuma take gaya masa in an jima zasu fito ita da Daddy zasu je asibiti. Bata ambaci sunan Safina ba amma ya fahimci duba Safinan zasu je yi, tunda suka shirya basu taba ambatar sunan Safina ba, they act as if ba ta yi existing a rayuwar su ba. Ballantana Mukhtar da har yanzu ba su ma bude babin sa ba. He then asked her yaushe zasu kuma haduwa? Yaushe zasu cigaba da maganar da suka fara. She said anytime ya samu damar fitowa daga gida yayi mata magana. Akwai wani abu da take son nuna masa, Daga haka suka yi sallama kamar ba zasu rabu ba sai dan lokacin sallar la'asar da yayi. Sannan kuma Daddy yana jiran ta zasu fita. Bayan ya tashi yayi sallah ne Mama ta jira shi ya sake komawa palo ya ci abinci sal kawai yayi zaman sa a falon yana kallon tv. A lokacin Mufida tazo dama kullum sai sunje asibiti ita da mijinta, ta zo ta saka shi a gaba da sannu har sai da ta fara bashi dariya. Sai ta zauna tana ta tattaba ciwukan jikin sa wai zata ga wanne ne yafi yi masa ciwo wanne ne kuma ya kusa warkewa. Ya ga alamar kamar fita zasu sake yi ita da Mama. Sai dai a lokacin da Mama ta fito da mayafin ta a jiki sai suka ji sallama an shigo falon, yana daga kai suka hada ido da Safiyya da Mommy. Sai da ya dan tsorata amma sai ya maze ya amsa sallamar kawai ya dauke kai. Zuciyar sa tana tambaya "me ya kawo su?" Mama tayi musu sannu da zuwa, Mommy ta zauna akan kujera Safiyya kuma ta zauna a kasa a gaban ta, daga ganinta kasan she is very uncomfortable. Sam ta kasa hada ido da kowa a cikin falon musamman Mama da kullum in ta ganta gani take kamar zata zo ta kwada mata mari. Sai da suka zauna sannan ta gaishe da Mama "Mama barka da yamma" mama ta amsa mata da "sannun ki"., Sai ta koma ta zauna tana jin kamar ta fashe da kuka, ta kasa gaishe da Muhammad ma. And to add to that sal Mommy tace "Safiyya ba ku gaisa da Muhammad ba, kin duba shi ma kuwa?" Safiyya ta dago kai tace masa "sannu., ya jikip" Ya danyi gyaran murya, she looked so sad that it breaks his heart "jiki da sauki, Thank you" Sai kuma aka yi shiru ana kallon kallo, kusan kowa a falon so yake yaji dalilin wannan zivarar a vanzu, except for Mommy, dan haka ita ta fara magana, "Afuwan Hajiya Zainab mun zo muku kai tsaye, na ga ma kamar fita zaku y" Mama tace "dama grin ku zamu je mu sake duba jikin Safina" Mommy tace "haka ne, kuna kokari kam wajen duba ta. Amma ni in magana tana damuna a rai na bana iva yin shiru akan ta sai na yi ta shi ya sa na kasa hakuri nace da Safiyya tazo ta rako ni inzo muyi maganar kawai kowa ya huta" Mama tayi gyaran murya tace "wacce maganar kenan Hajiya Sa'adatu? Ina fatan dai lafiya ba jikin Safina bane? Wani abun likitocin suka ce?" Mommy tace "a'a jikin Safina da sauki, ai dazu ma kum ganta, tsagewar kashin ce ma matsalar da tuni sun sallame ta ita ma" ta danyi shiru sannan tace "akan Safina din ne dai, akan kuma jikin na ta. Nace bara inzo inji wanne mataki kuka dauka ko kuma zaku dauka akan sa" ta fada tana nuna Muhammad "naga alamar fa Hajiya Zainab ko fadan kirki ba ku yi masa ba, Ni kuma ba zan iya ja baya inyi shiru ina kallon sa bayan ga abinda yayi wa yarinya ta ba, Gashi shi har an sallame shi daga asibiti zai cigaba da rayuwar sa ita kuma tana can tana fama da tarin injuries da kuma bakin ciki a zuciyarta, Ko hakuri ma fa bana jin yaron nan ya bata. Na san kun dauki nauyin hospital bills da komai har abinci da ruwan da zamu sha a asibiti kunyi providing but still she needs justice. In ba'a yi masa hukunci ba nan gaba abinda yafi haka zaiyi mata. Watakila gawar ta za'a kawo min nan gaba". Mama tace "Hajiya Sa'adatu. Da kin san wannan maganar zamuyi ai da mun sallami yara sai muyi ta mu kadai ko kuma da shi Muhammad din, amma wadannan kannen sane bai kamata ake maganar matsalar auren sa a gaban su ba" Mama tace "Safiyya ta san komai ai. Ina sane na taho da ita zuwa gaban sa dan ta kara sanin komai, so nake ta san duk irin halin kuncin da yar uwarta take ciki akan sa. Dan ta kama kanta ta guje wa aikata irin kuskuren da yar uwar ta tayi ta san irin mijin da zata kawo in ta tashi aure". Mufida ta take zaune a gefen Mama tace "Mommy Yaya Muhammad is the best mij da kowacce mace zata samu, Mij ne irin wadda kowacce mace take mafarkin samun irin sa. Dan Allah Mommy kar ki fadi maganar da za'a mayar miki". Mommy tace "gashi nan al kina mayarwar. Ni dai ban gani ba, Babu abinda Safina ta samu a gidan auren ta sai bakin ciki da bacin rai. Kun kalle ta kunga yadda ta koma kuwa? A haka take sanda aka yi auren?" Mama ta juya tana kallon Mufida, sai Mufida ta dauki wayarta ta mike tayi ciki, Safiyya ma sai ta mike zata yi waje, amma sai Mommy ta dawo da ita, "dawo ki zauna. Ina sane na taho da ke ai. Darasi nake so ki dauka." Safiyya ta koma ta zauna hawaye ya fara taruwa a idonta. Muhammad da da yake adan kwance a jikin kujera sai ya mike ya zauna dai dai, Mama tayi sauri ta kalle shi "kar kayi. Kar inji muryar ka" sai ya koma yadda yake ya zuba wa Safiyya ido. Sai Mama ta dauko wayarta tayi kira tace "Haruna driver kana kusa? Eh, dan Allah dan je gidan Gidado, eh inda matarsa take, akwai kanwar matar Ramla a gidan, ka dauka min ita dan Allah yanxu ka kawo min ita gidan nan, da sauri Please. Na gode" sai tayi gyaran murya tace "Okay, Hajiya Sa'adatu. Bara muyi maganar. Tabbas nayi wa Muhammad fada, har yanzu kuma fushi nake yi da shi bamu shirya ba kuma nayi niyyar sai ya gyara halinsa sannan zamu shirya. Amma fadan da nayi masa nayi masa shine akan abinda yayi. Ba wai akan abinda bai yi ba. Muhammad ya mari matarsa tabbas, kuma haka din babban laifi ne wanda ban taba tsammanin zai aikata ba and I am very much disappointed in him, amma bai ture ta da mota ba" Mommy tace "Okay abinda ya gaya miki kenan ko? Abinda ya gaya miki kenan ke kuma kika goyi bayan sa. Bayan kuma kinyi min alkawarin zamuyi bincike zaku gano gaskiyar lamari. To idan bai ture ta ba ta yaya taji raunukan da suke jikin ta a yanzu, ta yaya cikin jikinta ya zube? Ita ta yiwa kanta?". Mama tace "ba zan ce ita tayi wa kanta ba amma bashi yayi mata ba. Ni na haifi Muhammad, kuma na san halinsa ciki da bai. Na san baya karya. Ban ce wai baya karya completely ba amma bai iya ba, ta yadda indai yayi in dai ka san shi sai ka gane karya yake yi. Na tabbatar kuma tunda ke kika haifi Safina, I am sure kema kin san dukkan halayen ta da suke bayyanannu tunda ni kaina da na dan zauna da ita a lokacin da Muhammad baya nan na san wasu daga cikin halayenta, Safina tana da karya. Na tabbatar kuma kin sani. She is defensive. Duk wani laifi da tayi ko kuma wan abu da take tunanin cewa laifi ne sai tayi karya dan ta kare kanta. Ko da kuwa abin dan karami ne as simple as waye ya bar tukunyar miya a bude, ballantana something as big as this". Mommy tace "okay, to kawai dan tayi wa Muhammad karya sai ta zubar da cikin ta?" Mama tace "bani da amsar wannan. Mu dan dakata kadan yarinyar can Ramla tazo. Ita ta kira ni a waya sanda abin va faru, ke ma kuma kince ita kuma ta kira ki. Dan haka ina saka ran cewa a gabanta abin ya faru. Sannan kuma yar'uwar Safina, so it's for Safina's advantage, bana jin zata yi mata karya" suka yi shiru gabaki daya, daga dukkan alama jikin Mommy ya fara sanyi. Suna nan zaune kowa yana magana da zuciyar sa suna jiran a kawo Ramlah sai Mommy ta nemi shiga toilet, Mama ta nuna mata ta tafi, sai kuma ta cigaba da zama tana kallon Safiyya da Muhammad. Safiyya tana zaune a kasa, kanta a kasa tana jujjuya wayar hannun ta, Muhammad kuma yana zaune akan kujera a kusa da Mama opposite din Safiyya ya zuba mata ido. And there is a sadness in his eyes that disturbed Mama, Tayi gyaran murya sai yay sauri ya dauke idonsa daga kan Safiyya, Tace "Safiyya" sal Safiyya ta dago kai ta kalle ta and immediately suna hada ido ta mayar da kanta kasa tace "na'am" sai Mama tace "akwai wani saurayi da na sani, iyayensa suka raba shi da wata budurwa da yake so dan suna tunanin zata cutar da shi, sai ya hada kayansa ya je ya dauke ta wai zasu gudu suje suyi aure a wani guri. Ma'ana ya zabe ta akan iyayen na sa. Me zaki iya cewa akan wannan saurayin?". Safiyya tayi shiru, daga alama ta rasa abin da zata ce, sai kuma daga baya tace "bamu yi dai dai ba Mama, Kiyi hakuri. Mun kuma gane kuskuren mu, Ba zamu sake ba" Mama tace "amma me kike tunanin ya saka shi yin hakan in the first place?" Safiyya ta sake yin shiru sannan tace "yarinta ce". Bayan Mommy ta dawo sai ga Ramla ta shigo da sallamar ta, fuskar ta cike da mamakin kiran da akayi mata. Ta gaishe su sannan Mama tace mata "yauwa Ramlah. Ina ta so ne dama in tambaye ki yadda akayi Safina taji ciwo. Muhammad dai mun san a mota ya fadi, Safina fa?" Ramia ta gyara zama tace "faduwa tay'" Mommy tace "kamar ya faduwa? A ina ta fadi?" Ramla tace "muna falon ta muna kallo tare sai muka ji shigowar sa gidan, sai ta tashi ta tafi bangaren sa, daga baya kuma sai naji ya fito ya tayar da mota ita kuma ssi naji tana ta kiran sa da karfi shine hankali na ya tashi sai na fito da sauri, sanda na fito sai na ga yana cikin mota ita kuma tana kokarin yi masa magana, kamar tana cewa kar ya fita, sai ta rike karfen bayan motar shi kuma sai ya ja mota da karfi shine ta fadi a wajen". Suka yi shiru gabakidaya sai Mama tace "da ta rike karfen ya juyo ya kalle ta, kin ga alamar ya san ta rike?" Ramla tace "gaskiya Mama ban sani ba. Motar akwai tint kuma glasses din a rufe suke dan haka ban ga fuskarsa ba" Mama ta sake tambaya "da ta fadi kuma bai tsaya ba" Ramla "bai tsaya ba, da gudu ya ja motar ai. Yana fita kuma naji karar motar a waje yay accident". Suka sake yin shiru sai Mama tace "shikenan Ramlah,. Shiga ciki ga su Aisha can kawar ki a kitchen, in kuma gida zaki koma kije sai Haruna ya mayar da ke" Ramla ta tashi da sauri ta shiga ciki. Mama ta juya tana kallon Mommy tace "tsautsayi ne ya faru amma ya hadu da ganganci. Ta yaya zata yi tunanin zata iya rike mota? Wannan dai ya wuce Allah ya basu lafiya baki daya, Allah kuma ya mayar musu da mafi alkhairin abinda suka rasa. Maganar mari kuma ya bata hakuri, kuma insha Allah nayi miki alkawarin makamancin hakan ma ba zai kuma faruwa ba, Kiyi hakuri" Ranar har dare Muhammad yana ta kiran wayar Safiyya amma bai samu ba. Ya tura messages ma amma babu response yana tashi da safe ma ita ya cigaba da kira amma still shiru, zuwa azahar ya kai matukar damuwa, sanda suka yi sallar la'asar ma kuwa daga Abba har Mama sun fahimci akwai abinda yake damunsa amma babu wanda yace masa komai sai ma maganar yaje ya duba Safina Mama tayi masa. Duk kuwa da cewa ita din taje da safe ta duba ta. Ya samu ya tafi bangaren sa kamar zai shirya ne zuwa asibitin sai ya sake kiran wayar Safiyya, bata dauka ba ya tura mata message "Please Safiyya don't do this, in ma nayi laifi ki hukunta ni da komai amma kar ki hana min jin muryarki" Shi gani yake yi maganar sa da Safina da akayi jiya a gabanta ce ta saka tayi fushi da shi. Sai ya sake kira. And she picked. Yayi ajiyar zuciya "na kusa in zama gawa.. This punishment is to severe for me Piya. Gwara ki saka ni inyi ta frog jump daga nan har Kaduna" sai yaji Muryar ta can kasa tace "I am sorry Baby, na kasa kiran ka ko amsa wayarka. I was sooo....." Sai kuma tayi shiru, yaji zuciyarsa tana bugawa da karfi, kamar kuka take yi, ya mike zaune daga kwancen da yake "Piya?.... Are you crying? Me ya faru?" Ta dan sai ta muryarta tace "I have been depressed tun jiya. I want to see you, can you come over please?" Tun kafin ta gama maganar ma ya mike "gani nan zuwa, kina gida?" Tace "eh. And Baby kana ji na? Please drive safely kaji? Ka taho a hankali. I can't take it in wani abu ya same ka, I cannot loose you too"., Yayi kokarin rage damuwar sa "naji. Zan taho a hankali, Just stop crying, We will talk about it idan na karaso". Ya cire kayansa tare da adjusting shoulder brace din da take ciki sannan ya saka kananan kaya saboda a waje akwai sauran rana, Cikin sauri ya shirya ya fita, a parlour ya tarar da Mama ace mata zai fita tace a dawo lafiya, ita tunanin ta asibiti zai je, yana fita ya dau hanyar gidan su Safiyya zuciyarsa cike da wasiwasin abinda ya faru da har ya saka ta serious kuka, dan yasan ita gwanar kukan shagwaba ce amma wannan bana shagwabar ba ne ba, Ranar ma bai shiga gidan ba a waje ya tsaya and he called her yace mata yana waje, ita ma bata ce ya shigo ba sai gata ta fito bayan yan mintuna, and he saw Malam Ya'u ranar ma a tsaye yana kallon su har tazo ta bude gaban motar ta shiga. Bai bi ta kan Malam Ya'u ba sai ya mayar da hankali kanta. Fuskarta tayi fari tas idonta ya kumbura. Yaji damuwar sa ta karu, "Piya? Lafiya? What happened?" Ta fara kokarin hana kanta cigaba da kuka tace "'jikin Daddy ya kara matsawa. Yau da safe ya kasa numfashi, sai da aka kaishi asibiti. They intubated him. Sai dazu muka samu ya fara numfashi, Ya dawo gida yanzu amma the doctor is with him for a 24 hours monitoring". Gidado yaji zuciyar shi tana breaking for her, ya san how much she loves her daddy. Ya fara bata hakuri "ya Salam, I am so sorry Safiyya. I am sorry you are going through all this, Allah ya bashi lafiya, Insha Allah zai samu lafiya kinji? Ki daina damuwa. Am sure shima ba zai so ya ganki cikin damuwa ba" ta goge hawayen da ya fara fitowa tace "kana gaya min hakan ne kawai dan ka kwantar min da hankali. But he is not getting better. Ciwon sa ba mai warkewa bane ba. Babu magani. Duk yawan kudin da nake dashi babu magani ballantana in siya masa. I have to stand back and watch him die a little bit at a time" bai gama gane maganar ta ba amma ya cigaba da kokarin kwantar mata da hankali. "Babu ciwon da bashi da magani Safiyya. Allah dai bai bawa likitoci samun maganin ALS ba for now amma hakan ba yana nufin babu maganin ba, and God can work miracle on him. Addu'a babu abinda bata magani kinji? We will pray for him. Allah zai bashi lafiya". Ta gyada kai kawai sai tayi shiru. Zuwa jimawa yace "do you think it is okay for me to go in and see him? Ina so inga jikin na sa" tayi sauri ta girgiza kai. "jiya da daddare bayan na dawo gida ya kira ni yayi min maganar ka" ta juya tana kallon sa "ya san abinda yake tsakanin mu, Ya kuma ce min in rabu da kai, Yace ba zai aura min kai ba. Yace bai yarda inje gurin wani ya aura min kai ba, Yace kuma in fito da miji inyi aure in the shortest time possible". Gidado yaji kamar duniyar sa ta ruguzo a saman kan sa. Shi da ya dauka Daddy zai fi musu sauki akan Mama da Abba, ta ina zasu fara kenan yanzu? And issue din Daddy is more sensitive saboda rashin lafiyar sa. Yayi shiru kawai yana kallon ta, yawun bakin sa gabakidaya ya kafe ballantana ya samu yayi mata magana. Sai ta kifa kanta akan dashboard din motar ta cigaba da kukan ta. Sun jima a haka tana kuka shi kuma yana kallon ta, sannan kuma a hankali ya dauko their forever rose da ya ajiye ranar nan a cikin motar, ya rike ta hannun sa yana juyawa yana karanta rubutun jiki sannan ya kamo hannun Safiyya ya saka mata ita a ciki ya hada da hannun sa ya rike. Ta dago fuskarta tana kallon sa, sannan ta kalli hannayen su and the rose in the middle, Tana ganin ta ta gane ta. Ta saka daya hannun ta share hawayen ta tace "you kept it" ya kirkiro murmushi duk da zuciyar sa a rikice take but he had to be the strong one yace "of cause I did, I cannot let go of it. I cannot let go of your love, I cannot let go of you. Kamar yadda kika ce, the love between us is a forever thing. It is stronger than anything da zai shiga tsakanin mu. We have dealt with enemies Safiyya, duk da har yanzu ban san details din battles din da kika yi fighting for to come back to me ba, amma na san cewa the worst is over. Na san cewa wadanda zamu fuskanta yanzu are the people that love us the most, and they want the best for us, kawai suna bukatar su fahimci cewa we are the best for each other. And that's what we will do. We will convince them. Ta cikin lumana dan bama son mu rasa albarkar su. We will show them how much we love and care for each other". Ta danyi shiru tana kallon shi and he saw yadda damuwar fuskar ta take washewa, and then a hankali tace "CCTV" ya dan bata fuska yace "what?" Sai ta girgiza kanta tace "nothing" amma kuma ya ga kamar 50% na damuwar ta ta tafi. Sai tace "there is something I want to show you. Something I want to tell you. Just drive I will direct you zuwa gurin" ya kunna motar tare da kallon gate din gidan "are you sure? Baba Ya'u zsi gaya wa Daddy mun sake fita, bana son Daddy yayi fushi da ke" tace "zai iya gaya masa amma ba yanzu ba. Yanxu ba zai samu ganin sa ba. And I want him to tell him" ya sake kallonta cikin rashin fahimta "why?" Ta danyi murmushi and in that smile he saw the stubborn Safiyya da ya jima bai gani ba. Suna fara tafiya ya ga ta juya ta kalli bayansu sannan ta dauki wayarta tayi kira "it is okay. You can go back. No babu damuwa. Yes I am sure" ta karasa maganar da authority. Ya sake kallon ta yace "da wa kike magana" direct tace masa "my body guards" da mamaki yace "body what?" Ta danyi murmushi "I will explain in a bit" sai kuma cikin damuwa tace "just promise me that koma me na gaya maka it won't change anything. Dan Allah" yayi ajiyar zuciya "I just told you that what I feel for you is a forever thing didn't I?" Ta dan kwanta a jikin kujerar tana kallon sa tace "I am just insecure ne kawai. I have been this insecure tun da nasan gaskiyar magana a kai na. Gani nake in na gaya maka gaskiya you will run away from me, Shi yasa tun lokacin na kasa gaya maka" ya danyi murmushi *wacce irl ce gaskiyar magana a akan ki din? That you are an alien from another planet, ko kuma ke jinsin aljanu ce ba mutane ba?" Ta dan yi dariya, yaji dadin yadda ta fara sakin jikinta amma kuma yana jin tsoron abinda zata gaya masa din, yace "I missed the way you smile and laugh" ta sake yin murmushi tare da rufe side din fuskar ta da hannu daya, yace "I like your finger and your nails" sai ta ja mayafin ta ta rufe fuskarta gaba daya ta kuma boye hannayenta a cikin mayafin. Yace "to in baki bude fuskarki ba ta yaya zaki nuna min hanyar da zamu bi?" Tace "ina gani ai a haka" yace "I like the sound of your voice too" ta fara buga kafar ta a kasa cikin shagwaba "ni ka bari, Allah" yayi dariya, trying to loosen the atmosphere more. A haka ta ringa nuna masa hanya har suka shiga wata unguwa sai kuma suka je gaban wani babban gida suka yi tsaya, gurin yayi kama da gidan gona saboda bishiyoyi da ya hango a ciki, and it also looked newly renovated dan tun daga waje yana jin kamshin pent and even the outside walls are newly painted. A saman gate din anyi rubutu da karafunan da akayi wa ado da fitulu an rubuta "The Oasis". Suka tsaya kawai basu ce komai ba, sai ta mika hannu ta danna horn din motar, wani mutum ya bude karamar kofa ya leko yana kallon motar, sai kuma ya fito ya rufe kofar ya taho inda suke, ta sauke window din side dinta sannan ta daga wa mutumin hannu, ya kalle ta sai ya koma ciki har da gudun sa sannan ya bude gate din ta ciki. A hankali Muhammad ya ja motar suka shiga ciki, yayi packing yana kare wa gurin kallo "wow, this looks amazing" tayi murmushi tace "thank you, let me show you around". Sai ta bude kofa ta fita shima haka. Shi duk a lokacin tunanin sa gurin Daddy ne, amma tana fitowa sai yaga ma'aikatan gurin sun taho suna ta gaishe ta sannan su gaishe shi, still ya cigaba da tunanin a matsayin ta na yar oga ne, sai kuma yaji wani da yaxo ya gaishe ta yana yi mata maganar abubuwan da za'a siya da kuma abubuwan da suka rage da za'a yi, kamar yana bata update, sai tayi kokarin dakatar da shi tare da ce masa zasu yi maganar later. Daga nan suka fara tafiya a cikin gurin shi da ita side by side, iskar gurin mai dad tana kada su, tsuntsaye suna yin wakokin su a saman bishiyoyin gurin. Suna tafiya tana yi masa bayanin ko ina da kuma abinda za'a yi a gurin, ya fahimci duk an gama gyaran sai abinda ba'a rasa ba, sai kuma dabbobin ne suka rage ba'a kawo ba, Suna tafiya suka zo wajen wata bukka, irin traditional bukka akayi but in a modern way aka saka flowers suka zagaye ta sannan aka saka kujeru a ciki, suka shiga suka zauna sai tayi shiru, kamar duk hankalin ta a tashe yake, yana kallon ta yace "uhum, ina jin ki. Kince zaki nuna min wani abu kuma zaki gaya min wani abu, what is it?" Ta nuna gurin da hannunta tace "this is it. This farm is what I wanted to show you" sai kuma tayi shiru, yace "it is good, gurin yayi kyau sosai and the business will be lucrative" ta sake yin shiru sai yace "menene kuma zaki gaya min?" Tace "abinda zan gaya maka shine it belongs to me. It is mine" ya bude ido cikin mamaki "WOw. Daddy ne ya baki" ta girgiza kai "not Daddy, but Ammie" "Ammie?" Ya fada cikin mamaki, ta gyada kai "yes, her. And wannan bashi kadai bane ba. It is not even among the most important. She….... She had ...." Sai kuma tayi shiru ta cigaba da jujjuya wayar hannun ta Ya jawo kujerar da yake kai closer to her yana leka fuskar ta yace "hey, it is me. Muhammad. You can tell me anything. What are you afraid of?" Ta dago kai tana kallon sa tace "am afraid you will leave me in ka sanj" ya girgiza mata kai "never. Kina jina? I will leave you no matter what" ta gyada kai sannan ta gyara zama. "A ina na tsaya maka a labarin da nake baka?" Yace "Ammie ta shigo Abuja ta sauka gidan Hajiya Maryama, Ita kuma ta dauketa a matsayin yarta" tace "okay, yanzu zamu cigaba...…” And then she told him labarin Safiya Haladu, irin fadi tashin da tayi da shekarun da ta dauka tana businesses daban daban har zuwa sanda ta koma Safiya Khalid and haduwar ta da Adam Muhammad da kuma risk din da ta dauka with the gold company and how it turned out. Zuwa shekarun da suka yi suna kafa business na hadin gwiwa da daukarkar da Allah yayi musu a cikin shekarun, problem din haihuwa da suka samu, her problem with her half siblings, haihuwar ta and her decision to gift her everything. Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Fifty Four: The Legacy 2 Not Edited…. Her🧕🏻 Two days ago... "good night, and don't forget to dream about me". And I did dreamt of him. Muna ta hira muna dariya. And it was the best dream da na yi a cikin shekaru, Washegari ban tashi da wuri ba sal around 12 na safe, Ina tashi da Muhammad na tashi a raina. Zuciya ta cike da tunanin sa, fuska ta dauke da murmushi. Da sauri sauri na shirya na sauka kasa dan inje in ga Daddy, duk da dai na san shima yanzu ba ya tashi da wuri. Ban ma tsaya yin breakfast ba, duk kuwa da Esther da take ta bina a baya tana gaya min ta shirya min favorite dina, Nayi mata godiya kawai na shige part din daddy, A raina ina tubanin ko ya huce? Ko yau zaiyi min maganar Muhammad? Ko kuma dai ni infara yimasa maganar? Ina shiga na ganshi tare da nurse din da yake zama dashi, sunayin maganganu a hankali amma suna gani na sai suka daina, kamar wata magana sukeyi da basa so inji, muka gaisa da nurse din na tambaye shi jikin daddy yace min da sauki, sai ya fita nikuma nazauna a gaban daddy tare da dafa guiwoyinsa ina kallon fuskarsa da murmushi a tawa fuskar, “good morning Daddy na” na fahimci yana kokarin cigaba da yin fushi da nine amma kuma ya kasa, ya dauke Kansa gefe yana Kallon tv yace "how are you?" Na dawo da fuskata inda tvn take nace "I am good, Ya jikinka ka?* yayi shiru bai ce komal ba sai ma ya fara kokarin daukan wayarsa da take gefensa. Na dauko masa wayar na bashi, sannan na tashi na dauko wani support machine da ake daura masa tun daga kafadar sa zuwa fingers dinshi wanda yake taimaka masa yayi amfani da hannun sa sosai, Na saka ma, still bai kuka ni ba sai yafara daddana wayarsa daga baya sai naga ya sakata a kunne yafara magana, najima a zaune a gurin ina jinsa yana ta waya da abokan sa, daga sun gama da wannan su koma yi da yi da wancan har dai nahakura ba tashi na fita Bayan nayi breakfast sai na sake komawa gurin Daddy, na tarar da shi tare da twins suna ta hira suna dariya, sai kawai na tsaya ina kallon su ina jin dadi a raina, Hassan yana ta zuba musu zance, ina shiga nima suka jani cikin hirar ta su, na karasa na zauna a gaban Daddy na dauki kafarsa daya daga kan karfen kujerarsa na dora akan cinyata ina shashshafa masa ita tare da jan yatsun kafar, sai muka fara maganar karatun twins, su wai sunfi son su dawo nan Abuja suyi karatun. Hassan yace "wallahi yaya bama jin dadin kanon yanzu tunda ba kwa nan, tunda kun ki komawa gwara mu dawo nan din muma. Gidan empty babu kowa" Daddy yace "in kun dawo nan aikin ku kuma fa waye zai yi muku?" Hussain yace "ni nayi retire" duk sai da muka yi dariya, nace "ya kuka fara karaya ne tun yanzu? Kamar ba maza ba? Ni plan dina shine a sama muku jami'a a kasar waje, sai ku ajiye akin ku tafi in kun dawo sai ku cigaba" Hassan ya fara murna "ni America zaki kaini yaya. Kuma kar ki hada ni makaranta daya da Hussain kar yaje yake ta min wa'azi a can". Daddy ya bude ido "au baka son wa'azi babana? To kayi wa kanka, a Kano zaka yi karatun" Hussein yace "yauwa Daddy, ka gano shi. Ni kam a kaini makarantar King Fahad a Saudiyya" Hassan yace "Allahu Akbar! Ya Sheikh ustaz Malam Ahmadu" Har Daddy sai da yayi dariya. Muka yi ta hira mai dadi kamar bamu da problem, sai daga baya yace min inje in shirya in an jima zamu fita ni da shi da twins muje mu duba Safina. Duk da dama su twins sunje da safe kafin in tashi daga bacci. Ban musa ba nace masa to. Daga nan na tashi na koma dakina, a lokacin ne naga kiran Muhammad, muka zauna muka yi hirar mu mai dadi na gaya masa zan fita zuwa asibiti. Daga nan na shirya da sauri dan kar in sake yin wani laifin a wajen Daddy, nayi sallar la 'asar sannan na fita. Hassan ne ya tuka mu a motar Daddy wadda take ajiye baya hawa, dama twins ne suke hawan ta yanzu idan sun zo gari, Hussain yana gefensa ni da Daddy muna baya, muna tafiya muna hira, and Daddy used the opportunity to talk to us about hadin kai da kuma son juna. "Be each other's keepers" he said. "ku kar kuga ita macece ku raina ta, ku yi mata biyayya kamar ni kuke bi, duk abinda zakuyi ku nemi shawarar ta. She is strong and she will take care of you, bani da shakka akan wannan. Ke kuma kar kiga su kanana ne ki raina su, ki saka su a cikin dukkan al'amuran ki, kiyi shawara da su a kan dukkan abinda ya shafe ki. In kinyi haka you will be enough for each other". Na kama hannun shi a rike da hannayena biyu ina jin wani nauyi a kirjina. He looked at me and smiled. Muna zuwa asibitin suka dauko kujerar Daddy a bayan motar suka dora shi akai sannan suka tura muka shiga ciki. Muna shiga dakin da Safina take muka tarar da wasu kawayen ta sunzo dubata, da suka gan mu sai suka yi mata sallama suka tafi. Na samu guri akan kujerar two sitters da take gefe a akin na zauna bayan na gaishe da Mommy, ina zama Mustapha ya shigo, ya je ya gaishe da Daddy sannan ya dawo ya zauna a kusa da ni, nayi kamar ban ganshi ba na dauko waya ta na fara daddanna wa. Daddy yaje har gaban gadon Safina ya duba ta, ta tashi zaune ta gaishe shi. Ya duba hannun ta da kafarta da taji ciwo sannan Mommy ta zo tana nuna masa fuskarta "ka ga marin da yayi mata? Ka ga irin cin mutuncin da yayi mata? Ko mu bamu taba dukan ta ba amma wani kato a can ya kusa ya kal ta lahira, Wannan yaron ba mutumin kirki bane ba Daddyn Mustapha. Wallahi ba mutumin kirki ba ne ba. Na tabbatar da kai ka bada auren Safina ba zaka ba shi ita ba. Na tabbatar da kai ne zaka yi bincike kuma zaka san halin sa. Ita dai Safina iyayen ta sun cuce ta, ita ma kuma ta cuci kanta tunda ita ta kai kanta gurin su. Amma yanzu ba zamu kuma irin wancan kuskuren ba". Duk mukayi shiru babu wanda yace komai. Safina ta fara kuka kasa kasa, Daddy ya dora hannunsa akan kafadar ta a hankali cikin muryar sa ta rashin lafiya ya fara rarrashin ta. "kiyi hakuri Safina kinji? Kaddarar ki ce haka. Amma za'a dauki mataki akan abinda ya far, zamu tabbatar haka ba ta sake faruwa da ke ba ko kuma da wani daga cikin yayan mu ba." Mustapha yace "wallahi dan Mommy ta hana nine amma da yaron nan dazu ba zai bar asibitin nan ba dan sai na karya masa hannu ko kafa" Daddy ya juyo yana kallonsa yace "ban amince ba. Kar ka taba shi. In ka taba shi kai ma ka zama irin sa kenan" Mommy tace "ai na gaya masa kar ya taba shi, matakin shari' a zamu dauka akan sa. Da dai iyayen sunce min zasu dauki mataki shi yasa nayi shiru na saka musu ido, amma yanzu naga basu da niyyar daukan wani mataki a kai dan haka mu zamu dauka" Daddy ya girgiza kai "'a ba za'a yi karar sa ba. Akwal martabar aure al a tsakanin su. A fara kokarin sasanta maganar a gida tukunna, sai in anga abin ya gagara tukunna sai a shigar da sharia ciki. Tunda duka da kuma ture wa da mota ai domestic violence ne". Ina jin su ni dai ban ce komai ba, A lokacin kuma na kara zargin daga Daddy har Mommy sun san tsakani na da Muhammad kuma suna fada min magana ne a fakaice. Suka cigaba da maganganun su Safina kuma ta cigaba da kukan ta sai kuma kawai naga Mommy ta mike, tace "ni in abu yana cina bana iya zama wallahi, Safiyya zo ki raka ni gidan su yaron nan, Mustapha zo ka kai mu. Gwara inje inji inda binciken nasu ya tsaya dan in san abunyi a akan maganar nan". Na dago kai da sauri ina kallon ta sai kuma na girgiza kai and ban san sanda nace "no Mommy, I don't want to go there" wani kallo da Daddy yayi min shi ya sa na mike na fita ba tare da na sake yiwa kowa magana ba amma ji nake kamar in ruga da gudu in samu mota in koma gida, like why? Me yasa zata je dani gidan du Muhammad akan rigimar sa da Safina? Al wannan maganar manya ce and I am not manyan Satina duk kuwa da cewa ni nayi mata kayan daki. Ina jin su suka fito ita da Mustapha suna maganganun su, yana bude motar nayi sauri na shige baya na zauna. Suka shiga gaba tana cigaba da mita tare da fadar maganganu akan Muhammad, sai na saka hannayena biyu na toshe kunnuwana na jingina kaina a jikin kofa. A haka muka je gidan raina a matukar bace, ni ban taba zuwa gidan su Muhammad ba sai ranar. Muna yin packing ta juyo tace min fito muje, na sake girgiza kai na kamar zanyi kuka "Mommy I rather stay in the car" tace "da a motar zan barki ki zauna ai da ba zan taho da ke ba. Ina sane na taho da ke din ai'". A dole na fito daga motar ina ji ina gani ta tusa keya ta zuwa cikin gidan, my mind was telling me to call one of my guards da na tabbatar suna waje ya zo ya kwace ni daga hannun Mommy ya mayar da ni gida. Muka shiga ciki, and I saw Muhammad da wata da na fahimci Mufida ce, sai kuma ga Mama ita ma ta shigo. Haka naje na zauna and I was literally forced to listen to maganganun su akan rigimar Safina da Muhammad har daga baya aka kira shaida ta kuma tabbatar da cewa Safina ce mai laifi concerning zubewar cikin da kuma raunukan da ta samu not Muhammad. Amma dai tabbas Muhammad ya mare ta. But that doesn't made me feel better dan kirikiri nake ganin kiyayya ta a idon Mama. Haka Mommy ta gama borin kunyar ta ta tashi muka fito, da zamu fito ta saka aka kira mata Ramla tace tazo mu tafi tare. Muka sake komawa mota muka juya zuwa asibiti. Mustapha yana ta tambayar yadda aka kare, Mommy ta fara "sun goyi bayan dan su. Wai ba da sanin sa bane ba. Har da kuma cewa wai marin da vavi mata ma ai ya bata hakuri. Kuma ta gaya min bai bata hakuri ba sai ma maganar banza da ya ke gaya mata". Na nemo ear piece na toshe kunnuwana har muka je asibitin, zuwa lokacin ana ta kiraye kirayen sallar magrib, muna zuwa muka tarar Daddy yana jiran mu na dauka juya wa kawai zamuyi mu tafi but he said "Safiyya kiyi wa Safina sallama" na ji kamar zan fashe da kuka, na je gaban gadon nace "zamu wuce. Allah ya kara miki lafiya" tace "Amen. Thank you" sai na wuce na fita da sauri ina jin alamar duk yan dakin ni suke kallo. ina zuwa mota sal gain Mommy nayi ta biyo mu, wai gida zata je ta kwana shi yasa ta taho da Ramiah ta kwana a wajen Safina. Ni dal har muka je gida ban sake magana ba, Muna zuwa na wuce dakina da sauri na kuma rufe kofa ta sannan na shiga toilet nayi alwala na fito nayi sallah, na rufe kofar ne saboda na san Mommy zata iya cewa zata shigo ta sake yi min irin maganar ranar nan ni kuma raina a matukar bace yake ina tsoron kar in gaya mata bakar magana. Ina jin ta tana taba handle din kofar amma nayi kamar bana kusa na cigaba da zama na akan sallaya. Ni na san har lokacin my mental health is not okay, in dai har zata zauna tana zagin Muhammad a gaba na anything can happen. Na tuna sanda Mukhtar ya zage shi a mota na bude kofa zan fita. Ina nan zaune har akayi sallar isha na tashi nayi sannan aka sake knocking kofa ta sai kuma naji muryar Esther. "Madam Daddy yana kira". Na ajiye charbin hannuna sannan na tashi na bude kofar na fita, na wuce Esther na sauka kasa. A dinning room na same su gabaki daya suna cin abinci, ina shiga Mommy tace "ina sane nace da Esther tace miki Daddy ne yake kira ai, gashi nan kin sauko, Tun dazu nake hawa ina miki magana amma o amsa baki bani ba" nace mata "ina sallah ne" sal kuma na juya gurin Daddy nace "Daddy ganj" ya nuna min kujera "ki zauna ki ci abinci tare da yan'uwan kj" na girgiza kai nace "na koshi" yace "ki zauna ki ci abinci nace" sai na ja kujera na zauna na zuba abinci a plate na fara ci kamar yadda ya umarce ni. Mustapha yana kallo na yace "wai ke me yake damun ki ne?" Mommy tace "fushi take yi, dan dazu na matsa mata ta shiga gidan surukan Safina" Hussein vace "Mommy to me yasa za'a matsa mata? Tun da ta nuna bata so ai da sai abarta ko" ta zabga masa harara tace "to uban iyawa, ka fi mu santa ne ko kuma ka fi mu sanin abinda yake dai dai. It was for her own good" Hassan yace "we just don't like seeing her sad. She have been through a lot. She should be happy" sai naji abincin da nake ci ya tokare a makogwarona, Hassan is right, I should be happy. But I am not. Ban kuma san ranar da zanyi farin cikin ba. Haka na cuccusa abincin, ina jin shi gabakidaya yana tsayawa a kirjina baya wuce wa ciki na, sal da na ga kamar zanyi wa kaina illa sannan a daina nci na cigaba da zama akan kujera ina kallon su har suka gama, Ina jin twins suna bawa Mommy labarin nace zan kai su kasar waje karatu, a take naji tana yiwa Mustapha maganar ya zauna da su ya taya su zabar makarantar da ta dace da fannin da kowa a cikin su yake son karanta. Daddy ne ya fara cewa zai shiga ciki ya kwanta, Mustapha ya tashi ya taimaka masa ya shiga dashi cikin part dinsa, ina ganin sun wuce na mike da sauri na fita nima na hau sama zuwa dakina. A hanya na hadu da Esther, sai na ga ta bini a baya amma bata ce min komai ba har na shiga dakina sai ta shigo ita ma sannan ta rufe kofa tana kallo na. Na tsaya ina kallon ta da alamar tambaya sai ta fara magana cikin inda inda "uhmm Madam, dama wani abu nake so in gaya miki" na zauna ina kallon ta with serious face nace "what? Wani abu ya faru ne?" Tace "I am not sure, but I just want you to be careful" na ji gaba na ya fadi, nace "careful about what?" Sai ta shigo ciki sosai ta zauna akan gado tana kallona tace "da akwai wani ex boyfriend dina, to yana ta so mu shirya ni kuma naki yarda" na cigaba da sauraron ta duk kuwa da cewa bani da interest in her relationship with her ex boyfriend, Ta cigabe "sal dazu, na ganshi a gidan nan bayan na dawo daga aiken da Daddy yay min, lokacin ba kwa nan kuna asibit!, I asked him me yake yi anan farko sal ya ki fada min yace it is confidential, Sal na cigaba da insisting sal naji. And in his attempt to get back to me sal ya gaya min" na gyara zama nace "ya gaya miki me?" Tace "dama yana aikin saka CCTV ne. To wal Daddy ne ya saka shi ya saka a ko'ina a gidan nan. Kamar Daddy yana zargin something us happening amma ba'a gaya masa, yana son sanin komal da yake faruwa a cikin gidan nan. Shine dazu ya fita da ku gabakidaya ni kuma ya aike ni dan ya bawa mai aikin damar yin aikin ba tare da kowa ya sani ba. He told me ya saka small cameras da ba za'a gani easily ba a koina a gidan nan except for bedrooms and toilets. Sannan yayl connecting komai zuwa wayar Daddy, duk abinda za'ayi yanzu a gidan nan Daddy zai gani kuma zai ji". Nayi shiru ban ce komai ba sai ta sake cewa "na gaya miki ne so that you should be careful in da akwai wani abu da ba kya so Daddy ya gani ko ya ji. Ni ma yanzu dole in rage saka kida a kitchen in ina aik™️" ta karasa tana dariya, Nayi mata murmushi "Okay Esther, Nagode sosal for this. I won't forget your kindness" tayi murmushi ita ma tace "you deserve it" har ta kai bakin kofa sai ta juyo tace "bazan gaya wa kowa ba bayan ke. And I wish Daddy zai kama duk me laifi a gidan nan". Bayan ta fita na jima a zaune ina juya maganar a raina sai kuma na tashi a kalli agogo sannan na fita na sauka kasa da sauri na tafi bangaren Daddy. Na tarar har an gama yi masa shirin kwanciya yana zaune akan gado da dan karamin Alqur'ani a hannun sa yana karantawa, sai na zauna a bakin gadon ina kallon sa har ya gama ya shafa, Da dauki Alqur'anin na ajiye a inda ake ajiyewa sannan na dawo na zauna Yana kaliona yace "Safiyya, akwai maganar da kike son gaya min ne?" Na sunkuyar da kaina sannan ace "Daddy fushi kake yi da ni ko?" Yace "akwai abinda kika yi wanda zai saka inyi fushi da ke?" nace "I am sorry Daddy, jiya nayi maka karya, nace zan je asibiti kuma ban je ba" ya daga hannun sa a hankali ya dago fuskata yace "tunda kin yarda baki je asibitin ba, ina kika je?" Na sunkuyar da ido na kasa ina wasa da hannu na, ya kira sunana "Safiyya" na dago kai muka hada ido sai na sake mayar da kaina kasa, yace * understand life has been hard, and cruel to you, I understand I haven't been as good a father as I planned to be for you, But you must put the past behind you and face your future. Na san cewa yanzu is too early in fara yi miki maganar aure, but I do not have time Safiyya. And I so much want to see you married and happy before I go, Ina so ki samu mutumin kirki mai hankali wanda zai soki kuma ya rike ki tsakani da Allah, wanda zai zame miki gata bayan babu ni ki aura, dan Allah Safiyya" nayi sauri na dago kai tare da rike hannunsa "Daddy don't beg me, abinda duk kake so shi zanyi, If you want me to get married I will get married, Ni dai so nake ka daina fushi da ni dan Allah, Na kwanta na kasa bacci. Ina cikin damuwa Daddy" na fada murya ta tana karyewa, yace "menene damuwar ki? Dan ina yin fushi da ke ko kuma akwai wata damuwar da ban?" Nayi ta kokarin fitar da maganar amma na kasa, sai daga baya sannan a hankali nace "Muhammad" yayi shiru yana kaliona sannan yace "wanne Muhammad din?" Sai naji na kasa kiran sa da sunan mijin Safina kamar yadda suke kiran sa da shi, Sal na gyara maganar "wanda muka je gidan su dazu" yayi ajjiyar zuciya, "mijin Safina?" ya fadi sunan da bana so din. Nayi shiru ban amsa wannan ba, sai ya sake tambaya "what about him? Me kike so ki gaya min akan sa?" Nace "uhmm, dama ..... Jiya da banje asibitin ba, muna tare da shi" yace "I know. Malam Ya'u ya gaya min. Abinda nake so inji shine menene a tsakanin ku da har zai bar asibiti a halin rashin lafiya, ya tsallake matar sa da iyayensa ya taho wajen ki?" Na cigaba da kallon yatsun hannu na sannan nace "Daddy, Muhammad shine ....... Shinake........Wannan maganar........." "Shi kike so zaki aura" yayi summarizing duk maganganun da nayi niyyar yi masa. Nayi shiru bance komai ba ina jin yadda zuciya ta take bugawa a kirjina. "Haka ne?" Ya tambaya, na gyada kai na ba tare da na kalle shi ba. Ya jima shiru yana kallona sannan yace "out of the billions of maza da suke duniyar nan Safiyya babu wanda yayi miki sai mijin da Safina take aure?" Naji hawaye ya fara taruwa a idona. "ba haramun bane ba tunda ku ba sisters bane ba, zai iya auren ku ya hada ku ku biyo Safiyya but common........ You are smarter than this Safiyya you are above this. Ta yaya ma hakan zata yiyu? Ta yaya ma kike tunanin zan aikata hakan?" Na dago kai ina kallon shi hawayen ido na yana karasa gangarowa kan kuncina, "Daddy shi nake so. I don't know anything else, I don't know yadda za'a yi ko kuma me hakan xai jawo I just know that I love him" ya dakatar da ni yace "and that is where you are wrong. Very wrong, Love is just not enough. Just because you love him and you think he loves you saboda yana dukan matarsa da wulakanta ta saboda ke doesn't make him the right choice. He is all shades of wrong for you. And ni ba zan aura miki shi ba". Na fara girgiza kaina hawaye na suna karuwa, "Daddy...." Ya daga min hannu, "dalilai uku ne ya saka ba zan aura miki shi ba kuma ban amince ko da ace gobe na tashi babu rai ki aure shi ba. Na farko saboda yana auren Safina, Safina tamkar yaya take a gare ki mahaifiyar ta ita take amsa sunan uwa a gare ki, Tun daga kan Sa'adatu har kan Hussain babu wanda zai amince da wanna shirmen da kike shiryawa and if you insist you will loose them just like you lost Ahmad, Dalili na biyu shine Muhammad ba mijin kirki bane ba, bana miki fatan ki auri miji mai irin halin sa, ance idan zaka aura wa yarka mill mai mata ka bincika kaga yadda yake treating matar sa ta gida saboda exact treatment zai yiwa second matar, Watarana kuma hannu zai daga ya mare ki " you provoked him, Dalili na blyu shine iyayensa, if you insist on marrying him har iyaye suka shige maganar they will dig and they may find out, abinda muka yi sacrificing a lot to bury, Gidan su kuma babban gida ne, How do you think they will treat you? How do you think, they will look at you?", Na rufe fuska ta da hannayena ina cigaba da kuka kasa kasa, Ya kamo hannun ya rike, naji yadda nasa hannun suka yi zafi yace "Safiyya, in daí na isa da ke ki hakura da yaron nan. Kiyi addu'a, nima zan yi miki addua, Allah ya baki wanda ya fishi, Sa'adatu is still insisting on Mustapha but I told her like I did before that ba zan matsa miki ba, But you should think about that too", Na karbe hannuna ina girgiza kai na tare da jin duk duniyar tayi min kunci, ji nake kamar numfashi na zai bar jiki na, Na zame zuwa kasan gadon na zauna sai kuma na mike nayi hanyar waje da sauri, ina jin shi yana kira na da muryarsa da take fita da kyar amma ban juya ba, ina zuwa dakina na tarar da missed calls din Muhammad a waya ta. Sai na zauna na rungume wayar a kirjina ina ta rusar kuka, gani nake yi babu abinda yayi min saura kuma a duniya. Babu wani sauran farinciki daya ragemin a duniya. Muhammad shine farin ciki na. Shi nake so Ranar kwana nayi ina aikin kuka. Kaina ya toshe na kasa yin tunanin komai ballantana in hango wa kaina hanyar da zata bulle da ni. Da assuba bayan nayi sallah ina zaune akan sallaya ta naji ana buga min kofa da karfi, sai da ma dan firgita sannan naji muryar Mommy tana kire na cikin tashin hankali, ban jira komai ba dan Daddy ne ya fara fado min a rai, na mike a razane na bude kofar, kallo daya nayi mata na san babu lafiya dan haka na wuce ta a guje ina harhada stairs na sauka kasa a dal dai lokacin da naga Mustapha yana turo shi akan kujerar sa zuwa waje, na karasa gurinsu a guje *Daddy!'" Na kira sunan sa da karfi ina jüliga shi amma baya motsi, a lokacin twins suka fito suma suna kokarin yin karo da juna, ina jin Mommy tana janye ni daga jikin sa amma kuka nake ina kiran sunan se "Daddy 1 am sorry" na fada a lokacin da ake saka shi a mota, Gabaki dayan mu haka muka dunguma zuwa asibitin, sai da muka ji sannan suka gaya mana cewa da sauran ransa numfashin sa yayi kasa yayi kasa sosai har yayi loosing consciousness, sai suka fara kokarin daidaita masa numfashin amma abin ya gagara, kamar hanyar da iska take bi zuwa lungs dinsa ne tazama weak takasa shigar da iskar, saida suka sake masa tube directly zuwa lungs dinsa sannan sukayi pumping oxygen ciki, a hakan ne numfashin nasa ya dawo, but they also kept him under sedative dan a samu numfashin ya dai daita kafin asan abinyi next Ranar naga tashin hankali, Dan ba zanma iya cewa ga a inda hankali na yake ba, bazan ma iya cewa ga abunda ake cewa ko akeyi ba nidai ina zaune a kusa dashi hannuna rike da nashi a gaba na akayi komai, sai bayan da aka gama ne sai ga uncle Ahmad ya shigo hankalin sa a matukar tashe, wannan shine gani na dashi tun ranar daya ajiye min takardar barni aiki. Na daki hannun Daddy na tashi na rungume shi, shima ya rungume ni hankalinsa yana kan Daddy sannan kuma ya sakeni ya karasa gaban sa yana shafa gashin Kansa, sai kuma ya tashi ya fice idanun sa cike da hawaye, sai wajen azahar Daddy ya fara farfadowa suka cire masa tube din sannan suka cigaba da monitoring breathing dinsa har sai da suka ga ya dawo dal dal sai abinda ba za'a rasa ba, Yayi kokarin yin magana amma ya kasa, doctors din suka sake saka shi ya koma bacci dan ya daina stressing kansa akan sai yay magana ko wani motsi. Daga haka doctor din mu yace a bamu shi mu tafi gida shi zai zauna da shi a gidan, dama kuma akwai nurses guda biyu da na dauka suke zama dashi tare da taimaka masa yin abubuwa, Mustapha ma kuma yana iyakacin kokarin sa. Sai bayan da muka taho a hanya sannan na fahimci menene ya faru, the nurse that was supposed to stay with him that night shine Mommy tace ya tafi zata zauna da Daddy, wai ita kuma sai bacci ya dauke ta a dakin ta sai da assuba sannan ta tashi, shi kuma ana tunanin tun cikin dare ya samu breathing issue din amma babu wanda yake kusa da zai taimaka masa a haka har yay loosing consciousness, sai da asuba Mommy ta shiga ta ganshi a haka, Sai naji na tsane su gaba ki daya, na tsani kaina nima. Ya za'a yi a bar shi shi kadai? How terrible must have felt sanda ya tashi yana neman taimako kuma babu wanda zai bashi? A gidan ma bacci aka barshi yayi, aka hana kowa shiga gurin sa sai doctor ma’aruf wanda yayi mana alkawarin yana tashi Indai ya fahimci babu matsala zai sanar damu muzo mu ganshi, sai alokacin na koma dakina, Esther tana ta bina tana rokona naci abinci tunda tasan ko breakfast banyi ba, nace takawo min daki sannan nashiga toilet nayi alwala nafito nayi sallar la’asar, na cigaba da kuka na agaban ubangiji, a lokacin ne naji karar waya ta, ni namanta ma ina da waya, nadauko ta a kusa dani pillow na tun inda na aliye ta jiya da deddare kafin iny/i bacci, anan na tarar da jerin missed calls din Muhammad da kuma messages din sa, na fatimei yay tunanin nayi fushi da shi ne akan zuwan de mukayi gidan su liya, Sal na Kira sti, aji dadin jin muryarsa amma kuma at the me time muryar ta sa ta tuna min da magangianun mu Daddy wya da dare, sai na nomi yazo in ganshi, yazo muyi magana. Babu jimawa yazo, ni kuma nayi amfani da lokacin jiran nasa wajen cin abinci da Esther sannan nayi wanka tunda kayan bacci ne ma a jiki na da hijab din sallah, na chanja kaya amma banyi kwalliya ba face turaren da na dan saka kadan, ko mai ban shafa a jiki na ba. Yana kira na yace yazo na fita da sauri amma sai na fara shiga gurin Daddy na tarar har lokacin yana bacci Dr tare da Hussein suna zaune a tare da shi. Sai na wuce na fita waje. A waje na same shi and I told him everything, yayi kokarin rarrashina tare da kwantar min da hankali duk kuwa da cewa shima na fahimci cewa nasa hankalin ya tashi. And I decided to continue with story ne da nake bashi. I decided to take him to the oasis and tell him the story of Ammie and her legacy. A Oasis din na bashi labarin, har zuwa kyautar da Ammie tayi min na kuma lissafa masa maya daga cikin abubuwan da ta bani. Na tsaya ina kallon expression din fuskarsa ina cigaba da jin faduwar gaba. Tun ranar da Daddy ya gaya min yawan abubuwan da na mallaka a duniya nake lissafin gaya wa Muhammad, har Allah yayi rabuwar mu ban samu courage din gaya masa ba, yanzu gashi mun sake dawowa. Ina tsoron kar ya guje ni saboda haka, dan nasan maza, musamman maza masu ji da mazantaka irin ta sa ba kowa ne zai so ace matarsa ta fishi arziki da daukaka ba. Yayi shiru yana kallona sannan ya girgiza kai "wait... Wait.... wait..... Just wait" nayi shiru duk da dama ba magana nake yi ba, ya cigaba da kallo na amma daga alama bani yake kallo ba hankalin sa yana yawo ne trying to get the clear picture of abinda nagama yi masa bayani. Zuwa can kuma vace "what?" Cikin mamaki. Na rufe idona na bude "I am sorry Muhammad. I never want to drag you into this. Nima duk ban san da wannan maganar ba sai daga baya. Kuma na rasa yadda zanyi in gaya maka. I was afraid you will leave me because of it. I am still afraid" na fada murya ta can kasa, ya dawo da hankalin sa gare ni, sannan na sunkuyar da fuskar sa kasa yana kokarin hada idon sa da nawa da na sauke kasa. "Hey sweetling, don't say that. Look at me" na dago ido muka hada ido da shi sai yace "I will never leave you kinji? Not because if this, not because of anything. In kinga na rabu da ke to sai dai in ke ce kika ce ba kya so na kuma" naji hankali na ya fara kwanciya, but still there is more to my news. But that will have to wait for another day, dan already na riga na yi plan din how to break that news to him. Na dan kirkiri murmushi nace "thank you. Nagode da soyayyar ka gare ni Yaya Muhammad" ya mayar min da murmushin sa mai kyau sai kuma ya daga kai yana hura iska ta bakin sa, he still looked shocked akan labarin nawa. But there is still more to that sai na cigaba. "It has been 22 years since the gift, it has been 20 years since her death, and things have changed since then. Everything have multiply" ya dawo da idonsa kaina yana kallo na na gyada masa kai "I now own almost everything da yake a sunan ta ita da Daddy. I own wealth that even I cannot comprehend. Sole ownership of two fully functional companies and a share in a lot of others. Including a hefty share in the gold company. And cash, lots and lots of cash". Ya sunkuyar da kansa yana kallon hannunsa sai ya dago yana kallona da murmushi a fuskarsa yace "tun ranar da na fara ganin ki, I have been calling you a rich kid, not knowing you really are a rich kid Safiyya" a danyi murmushi tare da girgiza kaina nace "I didn't know then. Har yanzu kuma ni kaina ban gama accepting maganar ba, Da ace za'a dawo da rayuwa baya ace kuma zasu tambayi ra'ayi na kafin suyi abinda suka yi I wouldn't have accept it, I don't want it, Nauyi ne beyond dukkan understanding dina, dukiya jarabawa ce and I have been through test often test tun kafin ma in San ina da dukiyar" nayi shiru sannan nace "Har yanzu a cikin jarabawar nake. And I don't know if I can pass this last one. I don't think I can lose you and Daddy at the same time". Sai ya kara matso da kujerar sa ya kama hannuna cikin rarrashi, na zame hannun ina goge hawayen da ya fara sauko min, yace "look at me Safiyya. Daddy will live longer than we have have ever dreamt of, and together we will convince him akan maganar auren mu kuma zai amine kinji. Na tabbatar miki da haka. Ki daina damuwa dan Allah". Na dan gyara fuskata ina jin dadin concern dinsa a gare ni nace "thank you Baby" yayi murmushi "wai ke waye ya kowa miki babyn nan ne?" Nace "ba ka so?" Yace "so kai... It makes me feel...... don't know how to explain it" na danyi dariya tare da juya idona "try..." Ya rage idonsa a kaina, na san irin kallon sai na rufe fuskata da hannu na yace "I will explain. Ki dan jira in gama yaki da Daddy da Abba da Mama, Sal inyi miki bayani dalla dalla, da manyan bakake" nace "na daina fada to" ya danyi dariya "ko kin daina yanzu I will make sure kin cigaba" na mike tsaye ina son ya daina min irin wannan kallon da yake yi min nace "come, let me show you something". Ya tashi ya biyo baya na muka sake jerawa muka cigaba da tafiya a gidan, kowa zuciyar sa cike da tunani, and I took him to the reservoir. Na durkusa a gabanta tare da dora hannu na akan murfin sannan ba tare da na kalle shi ba nace"she died here" va durkusa a kusa dani cikin confusion yace "who?" Na juyo ina kallon sa nace "Ammie" ya bude ido cikin mamaki sannan ya kalli reservoir din ya kuma kallo na, and I told him yadda mutuwar tata ta kasance. Har na gama bai ce komai ba. Jikinsa yayi matukar yin sanyi dan da kyar yake daga kafarsa yana jerawa da ni muna tafiya, Daga zuciyar sa har jikinsa duk sunyi sanyi matuka, Muka sake dawowa inda motarsa take sai nace "I need to get back home yanzu. Bana son Daddy ya farka ya ga bana kusa har kuma ya gane cewa na fita tare da kai" ya gyada kai da sauri cikin fahimta, Sannan ya bude motar muka shiga tare muka bar gidan gonar. Komawa gidan kusan in silence muka yi ta, lost in our thoughts, Na san dama maganar dukiyar ta dole zata buge shi kuma zai bukaci lokaci yay digesting maganar and comes to term with it, duk da dai maganganun sa sun karfafa min gwuiwa da kuka nina min cewa ba zai gudu ba, A kofar gida ya ajiye ni muka rabu tare da alkawarin zamuyi waya. Bayan ya kara yi min was kalaman kwantar da hankalin. Ana ta kiraye kirayen sallar magrib na shiga cikin gidan, direct part din Daddy na wuce na tarar Hassan yana yi masa alwala. Na karasa da sauri gaban sa "Daddy" na kira sunansa, ya danyi gyaran murya yana kokarin yin magana sai na girgiza masa kai tare da saka dan yatsa na a kan lebe na alamar yayi shiru, ya danyi min gajeren murmushi sannan ya kammala alwalar sa, na fita a lokacin da yake kokarin tayar da sallar daga kwance. Nima daki na na shiga nayi sallar tare da jero adduoin neman zabin Allah akan lamura na, daga nan sai na kuma komawa grin Daddy na zauna ina kalion nurses din suna saka masa drip wanda zai yi serving a matsayin abinci tunda a yanzu ba zai iya cin abinci ba., Bayan sun gama sun bamu guri sai muka zauna a tare da shi har Mommy muna ta yi masa hira, duk da baya bamu amsa amma yana ta bin mu da ido har daga baya bacci ya sake dauke shi. Sai bayan yayi bacci na koma dakina na tarar da missed calls daga gurin Muhammad da kuma gurin Aunty Hajjo, aunty Hajo na fara kira sai tace "ke ba kya kiran mu sai mun kira ki ko Fiyya?" Nayi murmushi kawai. Kusan kullum sai tayi min wannan mitar, ni kuma ina jin nauyin kiran ta ne kawai. Na gaishe ta tace "dama wani abu zan nuna miki" sai na katse kiran a kira ta video call duk kuwa da already na san abinda zata nina min din. Tana dauka kuwa shi na gani, Yana zaune a cikin play pen dinsa kayan wasa sun zagaye shi, Na bude baki cikin mamaki, ya zama katoto, yana ta mika hannu zai kamo wata ball mai kyalli da take makale a saman pen din, Nace "aunty Hajjo har kun kafa zama ashe?" Tace "muna koya daj" tana fada kuwa ya tafi da baya ya fada kan kayan wasan na sa. A tare muka yi dariya ni da Aunty Hajjo, shi kuwa ko a jikin sa sal ya cigaba da mika hannu still zai kamo ball din da yanzu ta kara yi masa nisa. Ta kai wayar kusa da fuskar sa, nace masa "hey", ya dan juyo yana kallona sai kuma yayi sauri ya kai wa wayar wawura yana kamata kuwa ya danna a baki, sai gani a cikin bakin sa. Da kyar Aunty Hajjo ta kwace, sannan ta matsar da wayar daga kusa da shi, ina ta murmushi nace "in ka lalatawa Aunty wayar ta sai ka biya ta" tace "mun saba fada akan waya ai" na tsaya ina kallon sa nace "wannan yaron Aunty kumatun sa kamar bread " tayi dariya "duk sanda kuka hadu idan kika dauke shi kuma zaki ce kamar block, irin 12 inches din nan". Sai kuma ta koma ta zauna a gefe muka cigaba da hirar mu. Ta riga ta san labarin Mukhtar da abinda ya faru, sai kuma na bata labarin rashin lafiyar Daddy da abinda ya faru dashi yau, ta jajanta sosai ta kuma kwantar min da hankali tare da alkawarin zata gayawa uncle Sufyan. Bayan mun gama waya sai na kira yallaban da already ya kara yi min two missed calls sanda muke waya da aunty Hajo. Yana dauka yace "hey" nace "hey you too" yayi dariya "yau babu babyn?" Nace “ nadaina ai” yace “ please, Dan allah, natuba” nace “ to sai kayi alkawarin kadaina tsokanata” yace “nayi, nayi alkawarin komai ma. Please kifada inji” nace “ to zan fada yanzu. Ka shirya?” Yace “ yes, say it please m” nadanyi murmushi kamar yana kallo na nace “Malam Muhammadu dan fillo”. Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Fifty Five: The Green Snake 2 Ina jinsa yana dariya nima na kife kaina a cikin pillow ina dariyar sai da ya gama yace "wallahi kinyi da dan halak, sai na rama. Zaki hadu da ni" na daidaita murya ta nace "sai dai ka rame ba dai ka rama ba. Haka kawai ka baro riga ka taho birni kazo ka takurawa zuciya ta" ya dan yi shiru kuma sai yace "you have been calling me dan fillo, ashe kema fillon ce. Shine kika boye min dan kar in rama" na girgiza kaina nace "| am not. I have never think of myself as fulani. Ko kalmar zo ban sani da fulatanci ba" yace "war.." sai kuma yayi shiru for sometimes sannan yace "na bawa kaina aikin koya miki fulatanci daga yau. We hardly speak hausa at home. And Mama zata ji dadi sosai idan taji kina fulatanci dan tana so sosai. Zata san cewa jikokin ta zasu iya" na danyi shiru sannan nace "you know as much as I do, ba iya fulatanci ko rashin iya wane zai saka mama ta so ni ko akasin hakan ba, So it doesn't matter" yayi ajjiyar zuciya "haka ne. But to ne yanzu the biggest issue is with Daddy. Because nasan case din is sensitive, dole mu ringa kiyaye abinda zamu ke fada ko kuma abinda zamu ke yi a gaban sa dan gudun bacin ransa. Any idea on how we can change his mind?" Na danyi murmushi dan already I have few ideas da a fara jan zaren sakarsu already. Amma ba zan gaya masa yanzu ba. Nace "not yet. Working on it. Yace "okay da kin samu idea tell me so that we can talk about it, a bangaren Mama da Abba I think I can change their mind, zan dai dan bukaci lokaci ne kawai. Weakness din Mama shine mu yayanta, like she can and will do anything for our happiness. I only need to convince her that you are my happiness shikenan magana ta kare" nace "inye dan gatan Mama. But what about Abba?" Yace "sai dai in Mama bata yi masa magana ba. Abba fa mijin ta ce ne" duk mukayi dariya nace "kamar ka fada a kunnen sa. Sai na gaya masa" yace "I am looking forward to ranar da zaki gaya masa din, I am looking forward to ranar da zaki zama free with them. They will love you, tunda na hadu da ke I always picture you as their in-law, and always picture yadda Mama zata ke pampering din ki with love kina yi mata shagwaba" na dan bude idona na na rufe a hankali nace "I can't wait either" Mun jima muna hirar iyayen mu sai mukayl sallama. Yace "about that baby thing, ni ta ban hakura ba. Ko ki fada ko kuma yau ba zanyl bacci ba kuma ba zan barki kiy| ba dan kiranki zan yi tayl a waya" nace "sal in kashe wayata al" yace "sai in taho inyi ta buga muku gate kuma ba zan tafi ba har sai kin fito kin ce min baby" nace "bismillah. My windows are sound proof, ko zaka kwana kana bugawa ba zan ji ka ba" ya langwabe murya "please, just say it" na makale kafada kamar yana kallo na nace "naki din" yayi a)jiyar zuciya "shikenan al. Na san matsayi na yau, Good night" nace "sweet dreams my Baby", Sai na kashe wayar da sauri ina murmushi, Da akwai wani magic a cikin soyayyar muni da Muhammad, no matter the trouble da muke ciki in dai muna tare sai muji kamar an dauke mana dukkan damuwa, in dai muna tare to everything else feels like a background noise. Nayi ajiyar zuciya ina kallon wayar sannan na dora ta akan kirjina na dora pillow akan ta na rungume ina cigaba da murmushi, Nayi bitar maganganun mu da muka yi and I understand dalilin da yasa yake ganin zai iya convincing Mama cikin sauki, saboda bai san maganar Mukhtar da amma yana motsa bakin sa da alama azkar yake yi. Na kama hannun sa na kai bakina nayi kissing sai ya bude ido ya kalle ni "good morning Daddy" a fada a hankali, ya gyada min kai kawai, nace "ya jikin?" Ya mayar da idonss ya rufe bai ce min komai ba sai na mayar masa da hannunsa kan cinyarsa a tashi ina tambayar nurse din ya yake ganin jikin daddyn. Yace "da sauki sosai Madam. But we will need a breathing machines on standby dan gudun kar a kuma samun irin wancan attack din." na gyada kai da sauri '"dr Ma'aruf yayi min magana jiya a asibiti, har na bashi go ahead to order it, yace guda biyu za'a siya ko?" yace "yes, abinda ya kamata kenan, akwai bipap machine, shi kamar mask ne da za'a ke saka masa kullum danbya taimaka masa wajen jan enough air, sai kuma mechanical ventilator da za'a ajiye just in case of another attack" nace "za'a kawo su insha Allah" yace "okay. Sai kuma maganar abinci, baya iya hadiye abincin da zai wadace shi yanzu, dole a fara feeding dinsa through a feeding tube. But zainiya cigaba da gwada ci da kansa din amma kuma sai muke supplementing through a tube dan kar yake zama da yunwa" na gyada kai duk da hawayen da yake kawowa idona, a raina nace "a feeding tube it is, dan my father will not die hungry", Na juya ina tafiya yana bina a baya yana cigaba da yi min bayanin yadda zasu ke Needing din nasa da kuma duk abinda suke bukata. Sai da muka kai parlour sannan na dakata har ya gama sai nace *kuyi magana da Dr Ma'aruf in ya shigo. Kace nace ayi duk abinda ya kamata" ya gyada kai "okay ma'am" gar na juya zan tafi kuma sai na dawo da baya ina kallon sa nace "will there be pain? Zai ji ciwo sosai?" Ya girgiza kai "no, Just discomfort kafin ya saba. The whole thing about ALS is that it is painless. Babu pain ko kadan" na gyada kai sannan nayi masa godiya na koma ciki, A dakina bayan na koma na kwanta nake lissafa wanna shine kusan machine na goma da za'a siya wa Daddy to help him with the most basic things that healthy mutum yaje yi cikin sauki. Health is truly wealth, Bayan power wheelchair dinsa da take taimaka masa wajen tafiya automatically ba tare da an tura shi ba, tana kuma ina yin kwana sannan ta hau karamin tudu kamar na bakin kofa da sauran abubuwan da normal wheelchair bata yi, akwai machine din da yake taimaka masa wajen transferring dinsa from the wheel chair to the bed da daddare and back to the wheelchair da safe, akwai wanda ake daura masa a hannu wanda yake taimaka masa wajen aiki da hannun kamar cin abinci da operating wayarsa da sauran basic amfanin hannu, Da akwai wani a toilet da yake taimaka masa wajen hawa toilet seat din da kuma sauka, da kuma tsaftace jikin sa in ya gama, da akwai na exercise, wanda ake dora shi kullum ya motsa dukkan jikin sa to avoid yankwanewa da nannadewar da jiki yake yi idan ba'a amfani da shi. Da akwai wani ma da muka yi order last week, wanda zai taimaka wajen amplifying voice dinsa yadda za'a ke jinsa sosai tunda yanzu maganar ta sa tayi kasa sosai, akwai wanda yake taimaka masa wajen yin tari ya kuma yi clearing airways dinsa tunda bashi da karfin yin hakan da kansa. Wadannan duk abubuwa ne da healthy mutane suke yin su kullum ba tare da sun biya ko kwandala ba. Ban iya komawa bacci ba, na jima akan gado ina saka da warwara, gabaki daya zuciya ta a dagule, daga baya sai na dauko wayata dan inga ko ina da meeting ko wani abu da zai dauke min hankali na and keep me sane, Sai naga sakon barka da tashi daga Muhammad "morning sweetling. Just want to put on a smile on your beautiful lips, with an assurance that today is going to be a good day insha Allah kinji? No matter what is going on in life I will always be by your side sharing the joy and the sorrow, Forever and ever. With lots of love from your Baby". Nayi murmushi sannan nayi dariya ni kadai kamar tababbiya. Sai kuma nayi masa reply "hey Baby. Ya jikin? Thank you for the smile, really needed it. Sending lots of love from a stupid heart crazily in love with you". Daga nan sai naji na samu karfin fuskantar ranar. Na tashi a shiga wanka na dauki lokaci ina wanke jikina da mayukan wanka na da suke karawa fata ta kyalli, laushi da santsi, Na fito daga shower na tsaya a gaban mirror din cikin toilet din ina goge jikina ina kuma kare wa kaina kallo, har yanzu ba zance na dawo yadda nake ada ba but na chanja sosai from yadda nake sanda na dawo daga Berlin, fata ta ta dawo color dinta na ainihi sai kyalli take tana daukan ido amma har yanzu ban mayar da kiba ta ba saboda har yanzun hakalina ba'a kwance yake ba, na tsaya ina kallon fuska ta da yadda tsarin komai yake a cikin ta, sai na sauke ajiyar zuciya ina godiya ga Ubangijin da ya halicce ta dan ko ni idan nibaka bawa ikon halittar kaina bana jin zan yi wa kaina kirar da tafi wadda nake da ita a yanzu. Na dan ja da baya ina kallon gurin da aka yanka a ciki na aka fito da Junior, na saka hannua hankali na taba gurin, ya danyi taurin da in ka taba zaka ji shi a hannunka amma a ido it is barely showing sai dai in kasan da shi dama and you are looking for it shine zaka gani, and it has been just 5 months, hakan ya sa na kara jinjinawa likitocin a bisa kwarewar aikinsu sannan kuma na kara tabbatar da abinda suka ce akan aikinsu baya barin scar. Cikina ma kuma bai nuna alamar cewa dan mutum ya zauna a ciki ba, ko dan bai karasa girma ba aka cire shi? Dan ko wata bakwai cikin Junior bai karasa ba sanda aka yi min aiki. Sai kawai naji ina jin tausayin sa, bai gama jin dumin cikin mahaifiyarsa ba bai kuma ji dumin ta a ranakun farkon rayuwar sa ba. Sai naji ina son ganin sa, just to hug him I little and assure him that I love him and that everything will be okay. Amma kuma na san zuwa na Berlin a yanzu wani abu ne da zan iya cewa is close to impossible, babu yadda za'a yi in iya tafiya in bar Daddy kamar yadda babu yadda za'a yi in iya daukan Daddy a halin da yake ciki in tafi da shi. Na sake sauke ajiyar zuciya sannan a hankali nace "I am sorry Adam, You are going to be okay", A daki na zauna na shirya cikin doguwar riga marar nauyi bayan na shafe jikina da mayukan da suke kara gyara fata ta, sai kuma na jawo system dina na koma kan study table dina na bude na fara going through abubuwan da ya kamata inyi a yau. Na ga cewa ina da meetings har guda biyu daya da rana 12 daya kuma da yamma 4pm. Sai kuma na mayar da hankali grin karanta wani breakdown da aka turo min na retailers dín kayan mu da yawan kayan da kowa yake siya a wata daga kamfani. Ina so ne zan yi musu kyauta ta bajinta dan in kara rike su gam a hannuna, Na gama dubawa sannan nayi deciding abinda zany musu a rubuta na tura wa marketing department, Ina cikin aikin Esther ta shigo ta gaishe ni tace "Madam breakfast fa yana kasa tun dazu, ko a kawo miki sama ne?" Na dan girgiza kai "kawo min coffee kawa'" ta bata rai "Madam, in ba kya cin abinci zaki fadi watarana" na daga ido ina kallon ta sai tace "so nake ki zama katuwa" na bata rai "I don't want to be katuwa" sal tayi dariyar yadda nake yatsuna fuska tace "to ki dal ci abinci please, Breakfast is the most important meal of the day. Ki samu ki ci protein sosai da breakfast, it will help you go through the day, ko da ace kin zama too busy to eat a complete meal to ba zaki rasa energy ba, Kuma breakfast baya saka kibar da ba kya so, tunda shi You will burn it down during the day ba karar dinner da ake ci a kwanta ba" na yi murmushi "thank you for the lecture. Now, bring my coffee" ta dan bata rai ta juya tana magana kasa kasa, da alama mita take yi. Na bi bayanta da kallo ima murmushi sai kuma wani tunani ya zo min na mike na rufe system din tare da na da karamin mayafi a kaina na fita. A stairs na wuce ta da sauri ina hada bibbiyu, ta biyo ni a baya tana haki, na juya nayi mata gwalo "idan da baki hada wannan kibar ba ba zaki yi haki for just coming down the stairs ba" ta bata rai tace "nima dai slimming din nan zan yi", A dining table na zauna tazo ta fara zuba min abinci tana cigaba da yi min lecture akan nutrition, "Idan kin ci da yawa ma you can always go to the gym and turn the fat into muscles" na bata rai "I don't want to have muscle" na fara cin abinci na ta zauna ita ma tana kallo na tana ta zabga murmushi. Ma juya ina kalion ta tare da yi mata alamar tambaya da hannuna sai ta girgiza kai "nothing Madam. I am just happy that you are in a good mood today. Kwana biyu baya duk fuskarki babu smile" nayi murmushi "someone put a smile on my lips early this morning, and I am going to hold on to it har dare" ta danyi dariya tana tafa hannu "wonderful. I am so glad madam. Zanyi zaman daki. Please take me with you" na bude ido "I said someone, ya akayi kika san namiji ne?" Tace "I know love when I see it, and you madam are in love"., Nayi murmushi kawai bance komai ba. A lokacin naji alamar wani ya shigo gurin, naga kuma Esther ta gyara fuskarta sannan ta tashi tsaye tana gaishe da wanda ya shigo din. Na juya na ga Mustapha sai na dawo da ido na kan abinci na na cigaba da ci. Ya karaso ya zauna Esther ta fara hidimar zuba masa abinci, ya kalle ni na dago kai nace "goodmorning" yace "how are you?" Ban amsa ba na cigaba da cin abinci na amma ina jin idonsa still a kaina sai yace "ci ba kiba dai inji hausawa sun ce asarar abinci ne" dariya ta kusa ta kwace min sai na mayar da ita, hakan ya sa na kusa kwarewa, Esther ta bar shi ya dawo gurina ya zuba min ruwa ta miko min, na karba na sha nagode mata nacigaba da cin abincin still ba tare da nace masa komai ba. Yana cigaba da kallo na yace “why are you laughing?” Na danyi kokarin bata rai nace “dariya kuma? Waye yake dariya” yabata rai “wai da” nakara kokarin danne dariya ta na cigaba da cin abinci na. Esther tagama zuba masa ta juya ta fita ta barmu mu kadai. Yafara cin abincin sa yana kallo na har lokacin sai kuma yace “akwai maganar da nake so muyi dama fiyya. I have been thinking of a way to get you alone Amma na rasa, kin san yanda kike yanzu, kin zama hukuma sai lallashi” na gyara zama na tare da daukan cup din coffee na ina karasa shanye abinda yake ciki, na daga gira nace “wacce maganar ce knan ?” Yayi ajiyar zuciya “maganar ai guda daya ce. It is about us. I don’t know why you are still shying away from the truth, chasing a dream that will mever come true” na ajiye cup din ina jin raina yana baci nace “haryanzu dai ban gane maganar ba. Kace about us. Wacce magana ce about us” yayi shiru yana noticing changing yanayin fuska ta yace “kin sani ai” na mike tsaye nace “akwai maganganu da yawa da na sani about us Mustapha, maganar sanda kake cin zalina a bayan mutane sanda muna yara idan na kai kara kuma Safina tayi karya ta kare ka? Ko maganar sanda kayi ta trying to sexually assault me in then threatened me cewa idan na fada sai kayi da gaske?" Ya mike tsaye, jikinsa gabakidaya yana rawa idonsa kamar zai fado kasa dan tsoro yana kalion hanyar shigowa gurin "shishsh, me kike cewa Safiyya? Me ya kaio wanna maganar kuma?" Nace "ban gama ba ai, akwai wata maganar kuma, maganar sanda bayan mun girma kake shiga dakina a dukkan opportunity da ka samu and begging me to let you do it ko da sau daya ne" ya tako da sauri zuwa gabana yay kokarin rufe min baki da hannunsa, fuskarsa cike da toro, na matsa baya da sauri na kuma cigaba da magana, "you told me babu wanda zai sani, you told me ko na fada babu wanda zai yarda, I had to find a way to protect myself from you Mustapha, Saboda kai komawa nay kamar yar daba, duk dakin da na zauna ina ajjye da wuka a gefe saboda kai, har yau akwai wuka a dakina saboda in kare kaina daga sharrin ka. You traumatized my childhood, and you traumatized my nights at my teenage Na kasa gaya wa Daddy saboda maganar tayi min nauyi, na kasa gayawa Mommy dan mahalfiyar ka ce kuma ba lallai ta yarda ba kamar yadda kace. But maybe this is the right time to tell them, Maybe in na fada musu a yanzu zasu fahimci dalilin da yasa na zarge ka akan abinda ya same ni. Kuma zasu fahimci dalilin da yasa nace bana son auren ka" ya sake kokarin rufe min baki, na juya da sauri na dauki wuka a cikin set din kanana wukaren da suke jere a cikin shelf din da take bangon dining room din "the next time you touch me will be the last time you have a hand". Ya yi taku biyu baya yana kara lekawa cikin parlour sannan ya juyo yana kallona. '"na riga na baki hakuri ai Safiyya. Me kike so in yi miki ne kuma? Kuskure ne da rudin kuruciya da kuma sharrin shaidan kuma babu wanda yake above mistake. Kuma ai banyi ba ko? To me yasa ba zaki yafe ki manta maganar ba? What do you want from me?" Nace "kaje ka gaya wa Mommy da Daddy cewa ka janye maganar aure na. In baka fada ba ni kuma zan gaya musu dalilin da yasa ba zan aure ka ba" ya fara jujuya kansa "Safiyya. Wannan maganar ai ba ta kai wadda za'a fasa aure saboda ita ba. I promise you ban taba yi ba, a kanki ma kuskure ne da rudin shaidan, I mean you are very beautiful and we live together and I was young and hot blooded. But that doesn’t mean….” Na katse shi “I don’t care about shaidan and all his sharri stuff. Kai kayi min laifi kuma kai nake hukunta wa by not marrying you. I may forgive you but I can't marry you. Make them understand that or I will”. Yayi shiru muka cigaba da tsayuwa muna Kallon juna. A lokacin ne muka ji shigowar Mommy, tun kafin ta shigo parlour muryarta ta karade gidan da Fada, Ya juyo yana kallona da sauri yace "I will do it, just don't talk about this again" ya fita da sauri ya taffi gurin ta. Nima fitowa nayi daga dinning din na tsaya akan steps din da ake takawa daga parlour kafin a shiga dinning din ina kalion kofar shigowa pariaur. Mommy ta shigo mayafin ta a hannu tana zazzaga fada "ban taba ganin mahaukaciya, marar zuciya a duniya irin wanna yarinyar ba. Da ace bata kama da ni tsaf zance chanja min ita akayi a asibiti. Ta yaya za'a yi ni yadda nake da wanna zuciyar amma ace ita tata kare ya dauke?" Mustapiha da yake kokarin daidaita yanayin fuskarsa yace "Mommy lafiya? Ke da waye haka?" Hassan daya biyo ta a baya da jakarta yace a hankali “ita da yaya Safina”. lta kuma Mommy tace "ni da wa kuma in banda waccan shashashar kanwar ta ka? Wai yarinyar nan ance za'a sallame ta yau na tashi da sassafe na tafi dan mu taho gida tare amma budar bakin ta wai ita gidan mijinta zata koma, Ko a ina mijin yake? Dan wancan fitsararren yaron dai ba miji bane ba. Kuma wallahi ni da ita ne" ran Mustapha ya baci "kuma Mommy kika barta ta tafi baki babballata a asibitin ba?" Mommy tace "bar ni da ita. Bar mishi aikin nayi. Jira nake yi yayi gunduwa gunduwa da ita ya watso ta waje kuma na gaya mata wallahi ba zan koma asibiti zaman jinyar ta ba sai dai ta tafi Katsina wadanda suka aura mata shi suyi jinyar ta a can. Haka kawai yara suna nema su haukata ni. Wannan yaron ya zamar min annoba a cikin gidan nan wallahi. Ya mayar min duk yaran sun zama mahaukata. Daga safinan har Safiyya da nake ganin kamar tana da hankali". Jin ta ambaci sunana sai nayi saurin yin baya zan koma inda na fito. Ban san ta ganni ba sai ji nayi tace "ina zaki je? Dawo nan" na juyo na dawo cikin falon na gaisheta "good morning mommy" tace "wanne morning din? Wacce Mommy din? Yaushe rabon da ki gaishe ni a gidan nan?” Nace "Mommy al ba kya nan ne shi….” Tace kin san bana nan ne? Na tabbatar baki sani ba kuma baki neme ni ba saboda ke yanzu kin zama yar kanki ko? Ba'a isa ayi miki fada ba sai ki dauki fushi da mutane. Ina daukan ki me hankali ashe kema shashasha ce irin Safina. To wallahi bari kiji in gaya miki, abinda kike nema will never happen. Babu ta yadda za'a yi miciji ya sare ni a kafa daya kuma in sake mika masa daya kafar. In zaki dawo hankalin ki ma ki dawo tun kafin lokaci ya kure miki. Shashasha". Sai na juya nayi hanyar stairs. Tace "ai ba ce miki nayi na gama ba" na juyo na dawo amma sai na zamu guri na zauna danna fahimci ba yanzu zata gama fadan ba. Ta kuwa cigaba yin abinta. Ni dai na zauna kaina a kasa, ina yi ina kallon agogo ina lissafin lokacin meeting dina yayin da ita kuma ta cigaba da juye fadan ta a akaina. Allah ya taimake ni sai ga Dr Ma'aruf ya shigo, shigowar sa ce ta saka tayi shiru ta amsa gaishe ta da yake yi sannan ya zauna ya miko min wata takarda yana yi min bayanin bills ne na dukkan expenses din da aka kashe a wanna karon da kuma kudin machines din da akayi order. Na dudduba tare da sauke ajiyar zuciya nace "same account da wanda na tuna muku last month?" Yace "eh" Na mike nace okay, zan hado maka da salaries dinku for this month, shikenan sai mu gama dasu. Yayi murmushi "that will be good. Thank you" A haka na samu na zame na hau sama kamar zuwa zany in yi transfer din amma kawai sai na ajiye takardar nayi kwanciya ta na rufe idona. I knew I have achieved something with Mustapha amma kuma maganar komawar Safina gidan Muhammad tana neman dagula lamari na. Ba wai na saka ran ba zata koma ba ne ba amma kawai da najinta koma din sai naji kishin ya motsa. Ni kaina ban san yadda za'a yi wannan lamarin ba. Na dai san kawai cewa ina son Muhammad. Ban kuma saukowa ba sai da na gama dukkan meetings dina da na gabatar online. Ina gama wa na rubuta wata takarda na tura e-mail din Uncle Ahmad sannan nayi refreshing na saka riga da skirt na atampa na daura dankwalin atampar sannan na saka mayafi na kuma feshe jikina da turaruka masu tsada na fito. Dakin Daddy na fara shiga. A zaune na same shi Dr yana ta yi masa wasu bayanai shi kuma yana gyada kal alamar fahimta, Na zauna sai da suka gama sannan na karaso na gaishe shi, Ya amsa min, yanzu muryar ta fito amma can kasa, Nayi murmushi, Dr yace "jiki alhamdulillah, Kar ki damu kinji?" Na gyada kaí tare da kara matsawa kusa da Daddy na rike hannunsa nace "Daddy zan fita, Zanje gidan uncle Ahmad. Yanzu zan dawo insha Allah", A idonsa naga alamar yaji dadin magana ta, sai ya danyi mun murmushi kadan, Ina fita daga parlourn a na dauko shades a cikin jaka ta na saka a idona, Ina fita harabar gidan naga guards dina sun tashi zasu tafi gurin motasu sai na kira su da hannu na, suka karasa and I said "I don't feel like driving today" da sauri daya ya koma ya kawo motarsu zuwa inda nake, daya kuma ya bude min baya na shiga sai ya zagaya ya shiga gaba kusa da dan uwansa muka tafi, A hanya na gaya musu address din inda zamuje, gidan uncle Ahmad, Na dauko waya ta na a duba naga missed calls from Muhammad amma sai na share shi, Haushin sa nake ji duk da bai yi min komai ba. Amma kuma sai nayi amfani da lokacin wajen saving number din sa da sunan da yake kai tun da "Pyar💕”na kuma bata lokaci wajen zaban hoton sa a cikin hotunan sa da nayi retrieving na saka akan number din sa, na kuma zabi ring tune mai dadi mai cike da kalaman soyayya na saka masa, sai dai still da ya Kira ni ban dauka ba. A raina nace *kaje Matarka tana gida tana jiran ka*. A kofar gidan uncle Ahmad muka tsaya muka yi horn aka bude gate muka shiga, amma sai na zauna a mota nace su tambaya suji ko mukhtar yana ciki, suka dawo suka ce baya nan sai na fita sannan nace musu idan ya dawo kar su barshi ya shiga ciki har sai na gama na fito. Ina shiga cilkin parlour da sallama naga Umma ta fito daga Kitchen. Sai kawai ta tsaya tana kallona. Na cire shades din idona na durkusa na gaishe ta. Ta amsa still fuskar ta da mamakin ganina sai nace "Umma ina su Salima, ina Uncle?" Sai ta kalli dakin Salima sannan ta juya ta kalli hanyar part din uncle Ahmad amma still bata de komai ba. Sai na mike tsaye nace *Umma uncle din yana kusa? Zan iya ganin sa?" Ta dan gyara fuskarta tana kokarin cire mamaki daga cikin ta tace "bara inyi masa magana. Salima tana cilki zaki iya shiga" nace "zan shiga, bara in ga uncle tikunna". Sai ta juya ta shiga part din uncle Ahmad da sauri, Ina nan zaune sai ga Yaya ya shigo, nay kokarin gaishe shi sai naga yayi min kallon banza ya wuce yana cewa *dama ke kika ajiye mana wannan bakar motar da wadannan bakaken mutanen a kofar gida kenan" ban ce masa komai ba sai ya shige dakin Salima. Yana shiga sai ga ta ta fito, ta tsaya a bakin kofa tana kallona kamar yadda nima nake kallon ta. *Fiyya" ta fada a hankali. Na dan yi mata murmushi "hello Salima" ta karaso cikin falon tana murmushi itama. Kafin ta zauna uncle Ahmad ya fito tare da Umma. Na mike tsaye cikin girmamawa sai da ya zauna sannan na zauna nima a kasa, Umma ta zauna a gefensa tana kallo na fuskarta da expression din self pity. Na gaishe da uncle, ya amsa min idonsa a kasa sai nace "'Uncle dama zuwa nayi in tuna maka da cewa Daddy ba shi da lafiya. You should be with him. He misses you. Na san kuma kaima kana missing dinsa" yayi shiru sai kuma yayi magana muryarsa tana rawa "me zance masa idan naje?" Nayi sauri nace masa "kace masa ya jiki? Sai kuma ku cigaba da maganganun ku yadda kuka saba" duk muka yi shiru sai na sake cewa "tun kafin ku san zaku same mu kuke tare, you shouldn't be apart because of us" Umma tace "haka ne. Nima na gaya masa, Kin gan shi nan kullum yana kwance a daki cikin damuwa. Amma insha Allah zai je in an jima* nayi murmushi nace "ke ma ya kamata kije Umma, Kera ai kanwar Daddy ce. Ya kamata kema ki je ki ga jikin sa zaiji dadi. Ban jima sosai ba saboda babu abin magana sosai., Sun kasa sakin jiki suyi min magana sai na mike nace zan tafi, amma sal na kalli Salima nace "ki zo mu tafi tare Salima. In sun je in an jima sai ku taho tare" ta juya ta kalli Umma sannan sai ta koma dal da sauri ta dauko mayafin ta ta fito. Sai da zan fita nace da uncle Ahmad "uncle na tura maka sako email dinka. I will appreciate a response as soon as possible. The management misses you. Tare muka koma gida da Salima. Muna ta hira sama sama sai dai daga dukkan alama ita ma tsintar kalimomi take yi wajen yi min magana, Mostly akan lafiyar Daddy take min tambaya ina amsa mata. Tayi magana akan wayata da take ta hasken kiran da Muhammad yake ta jera min. ana ta kiran ki fa* na kalli wayar "share shi kawai" "shi?" Tace tana murmushi, nayi murmushi kawai bance komai ba sai ta dau wayar tawa da wani kiran ya shigo ta amsa ta saka a kunnen ta, na dago kai tare da bude ido ina kallon ta cikin mamaki. Sai naga tayi dariya tana rufe bakin ta da hannun ta sannan tace ba ita bace ba. Kanwar ta ce" eh muna hanya ne, naga kamar kayi laifi ne kana ta Kira ank dauka shine na taimaka maka na dauka* *okay to gamu nan karasowa" ta fada dai dai lokacin da muka sha kwanar shiga layin mu. A take na hango motar Muhammad a tsallaken gidan mu. Na juya ido na sannan na dauko shades dina na mayar dasu ido na nace da driver din ya tsaya a waje, muna tsayawa Muhammad ya bude motarsa ya fito ya tsaya a gaban ta tare da saka hannayensa a cikin aljihun sa. Na cigaba da zama a motar ina kallon sa, yayi kyau sosai cikin dinkin shadda ruwan toka mai duhu, rigar mai kananan hannaye ce wadda ta fito da damatsen hannunsa da naga sun kara girma fiye da yadda na san su, Fatarsa tana kyalli, iska tana kada yalwataccen gyararren gashin kansa. Salima ta taba ni sannan tace min a hankali "he is hot" nayi murmushi sannan na bude kofa na fita, a tare security din suka fito sai nace musu su wuce ciki kawai, I purposely cat walked toward him. Irin tafiyar da na tabbatar ta karasa susuta sauran tunaninsa. Sai dai yadda ya zuba min ido ya saka naji ina kamar zan fadi amma na samu da kyar na karasa inda yake. Ya danyi gyaran murya yace "you look stunningly beautiful. You took my breath away", Sai na daga gira na dauke kai gefe daya. Ya zagaya side din da na juya fuska ta tare da hade hannayensa a guri daya yace "ban san laifin da nayi ba. Whatever it is. Na dauki laifin 100 percent and I am sorry" na murguda masa baki sannan na sake dauke kaina "ni gida zan shiga yanzu" yace "not until you tell me me nayi" nace "ya kamata kai ma ka koma gida, Matarka tana jiran ka., Gwara kaje da wuri kar ka yi laifi" and I saw him smiled har sai da hakoran sa suka bayyana "my sweet Piya" ya fada a hankali. Na juya ba tare da nace masa komai ba zan tsallaka in shiga gida sai ya biyo ni ya sha gaba na sannan ya saka hannu na cire shades din idona "there is no way da zan koma gida ba tare da na kalli idon ki ba" na watsa masa harara trying so hard not to smile and kamar ya sani sai cewa yayi "now smile" and my stupid heart obeyed her master and I smiled at him, har da lumshe ido da budewa. A hankali yace “much better” sannan ya mayar min da shades dina yace “now I can go home and eat” yajuya yana tafiya da baya da baya yana kallo na har sai da bayansa ya taba motarsa sannan ya juya ya shiga ciki, blew me a kiss. Maman Maama ✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA ❤️‍🩹 Episode Fifty Six: The Talk Har na shiga gida da murmushi a fuskata, ina jin sansa a raina sosai sannan kuma at the same time ina jin haushinsa saboda komawar matarsa gidan sa, sai dai ni kaina nasan kishi ne ya saka ni jin haushin ba komai ba, and I asked myself "idan auren ya tabbata, am I ready to share him with Safina?" nayi sauri na kawar da wanna tunanin daga raina sannan nayi replacing dinsa da tunanin ciwon Daddy. Part din sa na wuce, na tarar yana zaune akan gado an saka masa pillows a bayan sa yana kallon tv yana sauraron karatun Alqur'anin da yake fitowa daga ciki, a hankali bakinsa yana motsawa alamar yana bin karatun. Na zauna a kasa a gabansa nima na cigaba da binsu. Sai kuma na tuna da Salima da muka zo tare, na dauki waya ta na tura mata message na gaya mata inda nake na kuma gaya mata zata iya shigowa. Ba'a jima ba sai gata nan ta shigo, ita ma ta samu guri ta zauna a gefe na ta cigaba da bin karatun kamar yadda ta tarar muna yi. Hussain ne ya shigo, ya sanar mana da cewa lokacin sallah yayi sannan ya dauko bowl yazo ya fara yiwa Daddy alwala, daga nan muka koma cikin gida muka tafi dakina tare mukayi alwala muka yi sallah, Bayan mun idar ne Salima ta tashi tana ninke sallayar da tayi using tace "wai safiyya da gaske wancan gayen kike jawa aji?" na danyi murmushi nace "shi waye da ba za'a ja masa aji ba?" Tace "ya hadu, nake gaya miki ya hadu, most girls will sell their kidney to have him look at them" nayi dariyar yadda tayi maganar nace "Allah ya basu sa'a, now forget about him mu sauka kasa mu ci abinci. I am hungry" muka sauko muka zauna a dining amma still bata daina maganar sa ba "dan kuka yi aure wato za'a ga kyawawan yaya" nayi murmushi kawai bance komai ba dan bana son yin maganar anan sai ta sake cewa "I wanted auren ki da Yaya Mukhtar ya dore, I was even picturing the nephews and nieces da zaki haifa min, amma Allah ya fi mu sanin dai dai. I wish you happiness, where ever and with who ever" naji dadin maganar ta nace "ameen, thank you", Na fahimci siblings din Mukhtar basu san gaskiyar abinda ya raba mu ba, ban san me iyayen suka gaya musu ya faru ma. Maybe shi yasa na fahimci yaya yana jin haushina dan shine ya tarar da yadda na daure yayansa tsirara akan gado. Da sauri muka ci abincin muka koma wajen Daddy, muka tarar Mustapha yana bashi abinci sai na zauna a gefen gadon ina kallon su har yace ya ishe shi aka ajiye bowl din. Salima ta gaishe shi ya amsa mata tare da mika mata hannu yana murmushi, taje ta saka hannunta a cikin nasa ya tambaye ta ina Salim sai tace yana school, da yake boarding yake yi a Lagos, sai ta kama yiwa Daddy hirar Salim din da irin dramar da suke sha idan yazo hutu, yana shekarar sa ta karshe ne yanzu. Daddy yana ta murmushi amma baya iya yi mata doguwar magana sai ita ce take tayi. Fahimtar da nayi cewa yau surutu take ji sai na fara tsoron kar ta bawa Daddy labarin hadadden gayen da yazo gurina dazu, Allah ya taimake ni dai bata bashi labarin ba har su uncle Ahmad suka shigo tare da Umma, bisa jagorancin Hassan. Suna shigowa Mustapha ya gaishe su ya fita. Na sauko kasa nima na barwa uncle Ahmad kusa da dan wan sa ya zauna ya gaishe shi, Daddy ya hade rai ya amsa sannan ya dauke kansa gefe, Umma ma ta galshe shi tare da duba jikin sa ya amsa mata itama babu yabo babu fallasa. Uncle Ahmad ya fara inda indar bashi hakuri dan ya fahimci fushi yake yi, Umma tana kokarin taya shi. Daddy yace "sai da Safiyya taje tayi maka magana sannan zaka zo ka duba ni?" Umma tace "yaje asibiti ai, lokacin baka sani ba", Daddy yace "bai san gida na ba kenan sai asibiti ya sani? Ke ma baki san gida na ba?" suka cigaba da bashi hakuri mu dai sai muka tashi muka koma cikin gida. A parlor muka zauna, su Mommy duk suna zaune banda Mustapha, na gaya wa Mommy zancen zuwan su uncle amma sai naga ta dauke kai tana bata fuska tare da magana kasa kasa. Muka cigaba da zama muna hirar mu da Salima tana bani labarin ita ma shirye shirye graduation dinsu da suke tayi, sai na samu kaina da tunanin nima fa da yanzu ina shekarar karshe a jami'a, ko zan koma watarana? Na samu kaina da tunanin kawayen da nayi a MD wadanda yanzu duk na watsar da su saboda yawan tambaya ta dalilin barin makaranta ta da suke yi da kuma tambayata ranar da zan dawo. Nayi ajiyar zuciya ina tuna shekaru bitu da yan watannin da nayi a makarantar, they were the most carefree days of my life, Muna nan zaune sai ga Mustapha ya shigo, yana zama sai naga ramla cousin din Safina da take gidan ta ta shigo itama tare da wadansu mata da na lura yan aikin Safina ne, na cigaba da baza idon ganin Safina sai naga bata shigo ba, na mayar da hankali na kan Mustapha sai naji yana. ce da Mommy, "gasu nan na dauko su, jikin ta zai gaya mata ai" Mommy ta bisu da kallo suna gaisheta tana amsawa dai dai sai ta kira Esther tace ta kaisu dakin da zasu zauna, tace da Ramlah ita kuma ta kai kayanta sama inda suke sauka in sun zo. Sai da suka tafi sannan tayi kwafa tace "zata san da ni take yi ne. Bani na kai mata yan aikin ba? To na dauke kayana, sai inga yadda zata kula da gidan da kuma kanta da hannu daya da kafa daya" Hassan da yake gefe yayi dariya "Allah sarki yaya Safina, yau ta taro match da Mommy" Mustapha yace "ita ta ja wa kanta ai, ni bana tausayin ta, har da hawayen ta kuwa da nace nazo daukan su, nace mata tazo mu taho tare amma yarinyar nan ta ki" Mommy tayi kwafa "ba zata zo ba ai, babu yadda banyi da ita ba nima fa, Dazu ma sal da na kira ta a waya na kare mata zagi tas amma kamar da dutse nake" Sai na koma kan kujera na kwanta na rufe har kafafuwana da hijab din jikina, jikina ya bani dalilin komawar Safina gidan Muhammad ba wai dan shi ko dan ita bane ba, ta koma ne dan ni, dan ta san hakan zai bata min rai kuma tana ganin cewa in dai ta fito to zata rage mana wahalar convincing iyayen mu akan maganar mu, zaman ta a gidan zai karawa shiga ta gidan wahala. Mommy dai ta jera tsaki da kwafa sun kai cikin charbi, aka jima tace "kuma wannan dan iskan yaron ba taimaka mata zai yi da komai ba wallahi, Allah ya sa ma ya zauna a gidan" babu wanda yace komai sai kuma tace "Hussain ka shirya ka je ka kwana a gurinta, yau dai kadai kafin gobe in san yadda zanyi da ita" Hussain ya bude ido da sauri "mommy ni kuma? Yanzu fa kika aika aka dauko su Ramlah sai kuma ki ce ni inje? Ni me zan iya yi mata a gidan?" Mommy ta hau shi da fada "eh kai din nace kaje, ko ba zaka je ba? Ai ba aiki nace kayi mata ba, kawai kwana zaka taya ta zuwa gobe mu ganj" Hussain ya tura baki yana magana kasa kasa tace "wallahi idan ba ka mayar da bakin nan dai dai ba sai nazo na fasa shi. Marar kunya fitsararre", Ya mike ba tare da yayi wa kowa sallama ba ya fita, sai Hassan ya tashi ya bishi, ta harari bayan Hassan din tace "na ga kashin awaki ma karewar hadin kai". Shigowar Umma ce ta katse mata maganar ta, ta kara hade rai, Umma ta zauna suka gaisa sama sama ta tambayeta jikin Daddy sai ta tashi tace Salima ta zo su tafi, nima na tashi na raka su waje har zuwa bakin mota nayi musu godiyar zuwan da suka yi, uncle Ahmad yace min ya ga sakona kuma ya gode, zamu karasa maganar ta waya, na gyada kai kawai suka tafi ni kuma a koma cikin gida. Amma sai na koma part din daddy, na tarar shi kadai ne, yana duba wani abu a wayar sa amma yana gani na sai naga yayi sauri ya kife fuskar wayar a kasa sannan ya bata rai kamar babu abinda yake yi, nayi kamar ban gani ba nima sai na zauna a gabansa na tambaye shi saukin jikinsa ya amsa min da cewa yaji sauki sosai, muka danyi maganar feeding tube din da za'a saka masa da kuma breathing machines din da za'a siyo. Sai kuma yace "Ahmad ya ce min kin mayar masa da aikin sa" na sunkuyar da kaina sannan na dago nace "I never wanted to take it. Na fadi maganar ne cikin bacin rai sanda na fahimci yana kokarin goyon bayan Mukhtar.but aikin sa nasa ne except idan shine da [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹SAFIYYA ❤️‍🩹 Episode Fifty Six: The Talk Har na shiga gida da murmushi a fuskata, ina jin sansa a raina sosai sannan kuma at the same time ina jin haushinsa saboda komawar matarsa gidan sa, sai dai ni kaina nasan kishi ne ya saka ni jin haushin ba komai ba, and I asked myself "idan auren ya tabbata, am I ready to share him with Safina?" nayi sauri na kawar da wanna tunanin daga raina sannan nayi replacing dinsa da tunanin ciwon Daddy. Part din sa na wuce, na tarar yana zaune akan gado an saka masa pillows a bayan sa yana kallon tv yana sauraron karatun Alqur'anin da yake fitowa daga ciki, a hankali bakinsa yana motsawa alamar yana bin karatun. Na zauna a kasa a gabansa nima na cigaba da binsu. Sai kuma na tuna da Salima da muka zo tare, na dauki waya ta na tura mata message na gaya mata inda nake na kuma gaya mata zata iya shigowa. Ba'a jima ba sai gata nan ta shigo, ita ma ta samu guri ta zauna a gefe na ta cigaba da bin karatun kamar yadda ta tarar muna yi. Hussain ne ya shigo, ya sanar mana da cewa lokacin sallah yayi sannan ya dauko bowl yazo ya fara yiwa Daddy alwala, daga nan muka koma cikin gida muka tafi dakina tare mukayi alwala muka yi sallah, Bayan mun idar ne Salima ta tashi tana ninke sallayar da tayi using tace "wai safiyya da gaske wancan gayen kike jawa aji?" na danyi murmushi nace "shi waye da ba za'a ja masa aji ba?" Tace "ya hadu, nake gaya miki ya hadu, most girls will sell their kidney to have him look at them" nayi dariyar yadda tayi maganar nace "Allah ya basu sa'a, now forget about him mu sauka kasa mu ci abinci. I am hungry" muka sauko muka zauna a dining amma still bata daina maganar sa ba "dan kuka yi aure wato za'a ga kyawawan yaya" nayi murmushi kawai bance komai ba dan bana son yin maganar anan sai ta sake cewa "I wanted auren ki da Yaya Mukhtar ya dore, I was even picturing the nephews and nieces da zaki haifa min, amma Allah ya fi mu sanin dai dai. I wish you happiness, where ever and with who ever" naji dadin maganar ta nace "ameen, thank you", Na fahimci siblings din Mukhtar basu san gaskiyar abinda ya raba mu ba, ban san me iyayen suka gaya musu ya faru ma. Maybe shi yasa na fahimci yaya yana jin haushina dan shine ya tarar da yadda na daure yayansa tsirara akan gado. Da sauri muka ci abincin muka koma wajen Daddy, muka tarar Mustapha yana bashi abinci sai na zauna a gefen gadon ina kallon su har yace ya ishe shi aka ajiye bowl din. Salima ta gaishe shi ya amsa mata tare da mika mata hannu yana murmushi, taje ta saka hannunta a cikin nasa ya tambaye ta ina Salim sai tace yana school, da yake boarding yake yi a Lagos, sai ta kama yiwa Daddy hirar Salim din da irin dramar da suke sha idan yazo hutu, yana shekarar sa ta karshe ne yanzu. Daddy yana ta murmushi amma baya iya yi mata doguwar magana sai ita ce take tayi. Fahimtar da nayi cewa yau surutu take ji sai na fara tsoron kar ta bawa Daddy labarin hadadden gayen da yazo gurina dazu, Allah ya taimake ni dai bata bashi labarin ba har su uncle Ahmad suka shigo tare da Umma, bisa jagorancin Hassan. Suna shigowa Mustapha ya gaishe su ya fita. Na sauko kasa nima na barwa uncle Ahmad kusa da dan wan sa ya zauna ya gaishe shi, Daddy ya hade rai ya amsa sannan ya dauke kansa gefe, Umma ma ta galshe shi tare da duba jikin sa ya amsa mata itama babu yabo babu fallasa. Uncle Ahmad ya fara inda indar bashi hakuri dan ya fahimci fushi yake yi, Umma tana kokarin taya shi. Daddy yace "sai da Safiyya taje tayi maka magana sannan zaka zo ka duba ni?" Umma tace "yaje asibiti ai, lokacin baka sani ba", Daddy yace "bai san gida na ba kenan sai asibiti ya sani? Ke ma baki san gida na ba?" suka cigaba da bashi hakuri mu dai sai muka tashi muka koma cikin gida. A parlor muka zauna, su Mommy duk suna zaune banda Mustapha, na gaya wa Mommy zancen zuwan su uncle amma sai naga ta dauke kai tana bata fuska tare da magana kasa kasa. Muka cigaba da zama muna hirar mu da Salima tana bani labarin ita ma shirye shirye graduation dinsu da suke tayi, sai na samu kaina da tunanin nima fa da yanzu ina shekarar karshe a jami'a, ko zan koma watarana? Na samu kaina da tunanin kawayen da nayi a MD wadanda yanzu duk na watsar da su saboda yawan tambaya ta dalilin barin makaranta ta da suke yi da kuma tambayata ranar da zan dawo. Nayi ajiyar zuciya ina tuna shekaru bitu da yan watannin da nayi a makarantar, they were the most carefree days of my life, Muna nan zaune sai ga Mustapha ya shigo, yana zama sai naga ramla cousin din Safina da take gidan ta ta shigo itama tare da wadansu mata da na lura yan aikin Safina ne, na cigaba da baza idon ganin Safina sai naga bata shigo ba, na mayar da hankali na kan Mustapha sai naji yana. ce da Mommy, "gasu nan na dauko su, jikin ta zai gaya mata ai" Mommy ta bisu da kallo suna gaisheta tana amsawa dai dai sai ta kira Esther tace ta kaisu dakin da zasu zauna, tace da Ramlah ita kuma ta kai kayanta sama inda suke sauka in sun zo. Sai da suka tafi sannan tayi kwafa tace "zata san da ni take yi ne. Bani na kai mata yan aikin ba? To na dauke kayana, sai inga yadda zata kula da gidan da kuma kanta da hannu daya da kafa daya" Hassan da yake gefe yayi dariya "Allah sarki yaya Safina, yau ta taro match da Mommy" Mustapha yace "ita ta ja wa kanta ai, ni bana tausayin ta, har da hawayen ta kuwa da nace nazo daukan su, nace mata tazo mu taho tare amma yarinyar nan ta ki" Mommy tayi kwafa "ba zata zo ba ai, babu yadda banyi da ita ba nima fa, Dazu ma sal da na kira ta a waya na kare mata zagi tas amma kamar da dutse nake" Sai na koma kan kujera na kwanta na rufe har kafafuwana da hijab din jikina, jikina ya bani dalilin komawar Safina gidan Muhammad ba wai dan shi ko dan ita bane ba, ta koma ne dan ni, dan ta san hakan zai bata min rai kuma tana ganin cewa in dai ta fito to zata rage mana wahalar convincing iyayen mu akan maganar mu, zaman ta a gidan zai karawa shiga ta gidan wahala. Mommy dai ta jera tsaki da kwafa sun kai cikin charbi, aka jima tace "kuma wannan dan iskan yaron ba taimaka mata zai yi da komai ba wallahi, Allah ya sa ma ya zauna a gidan" babu wanda yace komai sai kuma tace "Hussain ka shirya ka je ka kwana a gurinta, yau dai kadai kafin gobe in san yadda zanyi da ita" Hussain ya bude ido da sauri "mommy ni kuma? Yanzu fa kika aika aka dauko su Ramlah sai kuma ki ce ni inje? Ni me zan iya yi mata a gidan?" Mommy ta hau shi da fada "eh kai din nace kaje, ko ba zaka je ba? Ai ba aiki nace kayi mata ba, kawai kwana zaka taya ta zuwa gobe mu ganj" Hussain ya tura baki yana magana kasa kasa tace "wallahi idan ba ka mayar da bakin nan dai dai ba sai nazo na fasa shi. Marar kunya fitsararre", Ya mike ba tare da yayi wa kowa sallama ba ya fita, sai Hassan ya tashi ya bishi, ta harari bayan Hassan din tace "na ga kashin awaki ma karewar hadin kai". Shigowar Umma ce ta katse mata maganar ta, ta kara hade rai, Umma ta zauna suka gaisa sama sama ta tambayeta jikin Daddy sai ta tashi tace Salima ta zo su tafi, nima na tashi na raka su waje har zuwa bakin mota nayi musu godiyar zuwan da suka yi, uncle Ahmad yace min ya ga sakona kuma ya gode, zamu karasa maganar ta waya, na gyada kai kawai suka tafi ni kuma a koma cikin gida. Amma sai na koma part din daddy, na tarar shi kadai ne, yana duba wani abu a wayar sa amma yana gani na sai naga yayi sauri ya kife fuskar wayar a kasa sannan ya bata rai kamar babu abinda yake yi, nayi kamar ban gani ba nima sai na zauna a gabansa na tambaye shi saukin jikinsa ya amsa min da cewa yaji sauki sosai, muka danyi maganar feeding tube din da za'a saka masa da kuma breathing machines din da za'a siyo. Sai kuma yace "Ahmad ya ce min kin mayar masa da aikin sa" na sunkuyar da kaina sannan na dago nace "I never wanted to take it. Na fadi maganar ne cikin bacin rai sanda na fahimci yana kokarin goyon bayan Mukhtar.but aikin sa nasa ne except idan shine da [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Fifty Seven; The Talk 2 Not completely edited, my tire is tired 😂 He sat like a stone as I told him all that has happened to me tun ranar birthday dinsa da muka je cin abinci restaurant, na bashi labarin gaskiyar abinda ya faru da ni a ranar da kuma duk abubuwan da suka biyo bayan hakan, nayi amfani da kalmomin da nasan zai fahimci abinda nake nufi ba tare kuma dana bayyana abubuwa masu nauyi ba. Sai da na dangane har ga labarin yadda naji maganar aurensa da Safina da kuma haihuwar Junior sannan da dawowata Nigeria. Na bashi labarin zargin Mukhtar da na fara yi, aurena da shi da kuma tabbatar da zargin nawa da nayi bayan auren zuwa rabuwar mu da conditions din da na dora Mukhtar din a kai dan kare martaba ta da ta Junior. Har na gama maganganun nawa bai ce komai ba. Ni ma kuma ban iya daga kai na kalle shi ba har sai da na kai aya dan bana jin zan iya hada ido da shi a yanzu, bana jin zan iya sake hada ido da shi ma gabakidaya. Jin ya cigaba da yin shiru tsahon lokaci bayan na gama magana sai na mika hannu a hankali na kama hannun sa da nake gani ta cikin hawaye na, na kuma yi kokarin kiran sunan sa, "Muhammad.......?." Naji hannun sa yayi zafi kamar na wanda yake cikin zazzafan zazzabi, Sai ya zame hannun na sa daga cikin nawa da sauri sannan kuma ya mike da sauri kamar wanda aka watsa wa wuta yayi hanyar fita daga falon. Na mike nima da saurin ina jin wani irin tashin hankali da fargaba suna mamaye zuciya ta. Na mike rigarsa tare da kiran sunansa cikin karyayyiyar zuciya "Muhammad……….." Ya kwace rigarsa da karfi sannan cikin wata irin muryar da ban san shi da ita ba ya fara magana "I will kill him.... I will kill him.….. I will kill him...." Na fahimci wa yake nufi da him din, hakan kuma ya kara tayar da hankali na, na sake shan gabansa da sauri ina kuka sosai a lokacin,"Muhammad dan Allah ka tsaya, Muhammad Gidado..." Na fada ina kokarin ganin ya kalle ni amma sai ya ture ni gefe daya ya saka hannu zai bude kofar sai na zagaye shi da hannayena na dora kaina a bayansa na kama kuka mai ratsa zuciya, Ya tsaya first, sai kuma ya dauke hannunsa daga jikin handle din kofar tare da kife kansa a jikin kofar, ina jin yadda dukkan jikin sa yake karkarwa da wata irin zuciya da ban san yana da irin ta ba. Mun jima a haka sai kuma ya juyo da sauri ya zagaye ni da nasa hannayen tare da kife fuskarsa a saman kaina ya kama kuka. Nima nawa kukan na cigaba, ban san adadin lokacin da muka dauka a haka ba,amma mun ci kukan mu mun gode Allah. Sai kuma ya sake ni ya zare hannuna daga jikin sa ya koma cikin falon ya zauna tare da juya fuskar sa gefe. Na fahimci baya son inga kukan sa ne, wai shi namiji, ni kuwa babu abinda ya dame ni in kuka yazo min a tsakiyar titi ma zan iya zama inyi kuka na in gama in tashi in tafi, wanda ya gani matsalar sa ce ba tawa ba. Na koma nima na zauna a gefensa, sai dai har lokacin yaki yarda mu hada ido nima kuma ban shirya yin hakan ba dan haka ban kalli fuskarsa ba nace "Please Muhammad, promise me one thing, dan Allah kayi min alkawarin ba zaka ko kalli inda Mukhtar yake ba. Please, wannan ita kadai ce alfarmar da nake nema a wajenka" ya goge fuskarsa yana girgiza Kai, sannan yayi ajiyar zuciya yace *I can't. I can't make a promise that I cannot keep" na zamo daga kan kujerar na sauko kasa gabansa "you can. Dan Allah. I went through a lot to keep you clean and away from all these. Please don't go and get your hands dirty by touching him. Daukan doka a hannun mu ba zata jawo mana komai ba sai......" Ya katse ni cikin fada tare da sake mikewa tsaye "kina nufin shikenan? Yayi a banza kenan? Kin barshi saboda kina da sayin zuciya and family dinki sun goya miki baya just because dan uwa ne shikenan kuma magana ta kare? Shikenan babu abinda aka yi masa babu kuma abinda za'a yi masa?" Na mike nima "akwai abinda nayi masa Muhammad. Na kai shi kara grin alkalin alkalai na kuma tabbatar zai saka min. Ina zaune ne kawai ina jira. Sakayyar da Allah zai yi min ta fi hukuncin da kowanne irin alkali zai yanke a cikin alkalan duniyar nan. In ka taba shi yanzu hukunci zai dawo kanka ne kai kuma. Saboda baka da wani ground na shari'a da ya baka damar daukan hukunci akan abinda aka yi min. Please Muhammad, yadida na bar maganar nan ka barta kai ma. Idan da ace da akwai wata hanyar da zan bi mu wuce wannan level din ba tare da na gaya maka maganar nan ba Wlh ita zan bi. Idan da ace xan iya cire maka zafin da kake jl a zuciyar ka da na cire maka shi. You have no idea courage din da nayi amfani da shi wajen zama inyi maka wanna maganar" Sai ya zauna a kasa a inda yake tare da dafe kansa da hannaye biyu a hankali ya ambaci "my God!" Nima sai na koma na zauna. Ya jima a haka yana rocking in one place sannan ya dago kai yana kallona yace "you know what hurt me the most in all this? It is the fact that you went through all these ke kadai, without telling me Safiyya, You went through all that alone" ya karasa cikin karyayyiyar murya. Nayi shiru ina jin sabbin hawaye suna zubo min, ya cigaba "You should have told me. You should have told me the moment it happened. You should have at least share all that burden with me but you chose to carry it alone. Saboda me? Saboda kina tunanin zan guje ki in naji abinda ya faru ko kuma kina ganin ban kai matsayin da zaki gaya min bane ba?" Ya karasa tambayar cikin fada, Na dago ina kallon sa, muka hada ido for the first time, idanunsa sunyi ja sun kumbura kamar zasu fado kasa, a hankali nace "i didn't tell you because I know exactly what you would do idan da kaji maganar" yace "and what is that?" Na lankwasa kai ina kallon sa hawaye yana bin fuskata nace "cewa zaka yi cikin ka ne. It would break you up to pieces but cewa zaka yi kai ne, cewa zaka yi naka ne Zaka yi hakan dan ka bani kariya kuma dan kayi forcing iyayen mu su bar mu tare". Yace "then why didn't you let me do that? Yes, that's exactly what I would have done. Da kin barni nayi hakan da duk bamu zo wannan matsayin ba. Da magana ta wuce tuntuni" nace "da kuma iyayen ka har yanzu suna kallon ka da abin. Zasu yarda muyi auren but they will be very disappointed in you maybe har karshen rayuwar su akan abinda baka aikata ba. Yan'uwan ka, abokan ka, abokan aikin ka duk wanda ya sani ba zai kuma yi maka kallon mutumin kirki ba. Sunan ka zai baci akan abinda baka yi ba. And that's something da ba zan taba yi maka ba a rayuwa" Ya rufe idonsa tare da kwantar da kansa baya ya jingina shi a jikin kujerar da take bayan sa. Sannan a hankali yace "so you chose to lie to me. You chose to tell me that kina da aure. "I am married and I love my husband very much" ya karashe maganar cikin dacin rai, sai kuma ya juyo da kansa yana kallona yace "do you have any idea how much that hurt me?" Na girgiza kaina "it wasn't the best decision I know, But I wasn't thinking clearly. Tun daga samun cikin nan har zuwa haihuwar sa bana cikin hayyacina, Babu wani decision da nayi making a cikin lokacin da yake mai kyau ne except not telling you the truth, I mean, I tried to give up the innocent child for a close adoption a kasar da bama ta musulmai ba" na sunkuyar da kai na sannan na dago nace "I tried killing myself, twice" ya bude ido sosai sannan ya gyara zaman sa yace "you told me kinyi kokarin cire cikin ko da a bakin ranki ne. Wannan ne second time din?" Na daga kafada nace "sanda kaje gidan mu ka gan ni tare da Mukhtar a mota, ya fita da motar, yana gudu a motar sosai and he said some bad words akan ka and I opened the door zan fita daga cikin motar". Ya zaro ido sosai tare da rufe bakin sa da hannayensa, Fuskarsa cike da tashin hankali. Nace "na gaya maka wannan ne kawai dan ka fahimta kuma ka yafe min maganganun da na gaya maka to break your heart dan ka rabu da ni" ya rike hannuna da sauri "ba maganar in yafe miki ake yi ba yanzu Safiyya. Promise me that you will never do something like that again" na gyada kai na "insha Allah", Sai kuma muka yi shiru for sometimes, kamar ya danyi calming down a little kuma ya dan fahimta duk da nasan sai yaje ya zauna ya tattauna da zuciyar sa sannan zai fahimta sosai ya kuma gane what he is getting himself into. Daga nan kuma zai gane abinda ya kamata ya gaya wa iyayen sa, daga nan kuma zai san idan iyayen na sa zasu yarda da auren na mu or not, tunda shi ya sansu ya san abinda zasu dauka da wanda ba zasu dauka ba. Mun jima a haka sannan ya ambaci sunana cikin sanyin murya "Safiyya" na dago kai na kalle shi sai na mayar da kaina kasa dan ba zan iya cigaba da kallon jajayen idonsa ba. "I am sorry all this happened to you. Duk da har yanzu ban yarda cewa rashin gayamin was the best decision ba amma na fahimci girman soyayyar ki gare ni and na fahimci kin yi making that decision ne with my wellbeing in your mind, and I really appreciate that. And I will never take your love, understanding and care for granted. Kinji? Amma ina so kiyi min alkawari saboda nan gaba, promise me you will never hide anything again from me. Through thick and thin, through joy and sorrow, for better or for worst, promise me we will always be together and look out for each other, Kiyi min wannan alkawarin kinji?" Naji wata soyayyar sa tana karuwa a cikin zuciyata, shi a gurin sa wannan abin da na gaya masa bai ma kai abinda zai saka yayi considering rabuwa da ni ba. Shi kara jaddada min soyayyar sa yake yi a gare ni. Dama kuma na riga na san haka. But I want someone else to know. Dan haka na sake tambayar sa cikin karyayyiyar murya "Muhammad kamar kana manta wani abu. Ina da da. Dan da na haifa ba tare da aure ba. Wannan dan will always be attached to me and to yayan da zan iya haifa nan gaba. In kace zaka aure ni hakan yana nufin abin zai shafe ka kai da yayan da zamu haifa nan gaba. Are you sure you want to........." Ya katse ni "I am more sure now than I have ever been. Babu abinda ya faru wanda yake laifin ki ko laifin shi yaron, kaddarar ku ce haka. Nima kuma soyayyar ki ita ce tawa kaddarar, kaddarar ki kuma ba ta rage ko kadan daga cikin tawa kaddarar ba sai ma karuwa da tayi. All I want to do now is to take care of you in tabbatar cewa ba ki sake zubar da hawaye ba sai na farin ciki" ,. Na goge hawayen da suke bin fuskata, wadanda already na farin cikin ne ma. Ya sake matsowa kusa da ni. Yace "I want to marry you Safiyya. Will you marry me?" Na daga kai muka hada ido, murmushi yaso ya kubce min amma sai nayi sauri na rufe fuskata da hannuna na gyara mood dina sannan na bude fuskata a hankali nace "no". Yayi shiru yana kallona fuskar sa cike da alamomin tambaya iri iri sai nace "I am sorry Muhammad. I am very sorry. This is the last part of maganar da zamu yi yau. And your answer is no. I love you so much, fiye da yadda kalmomin bakina zasu iya furtawa. Ba ni kuma da shakka akan son da kake yi min musamman yau da ka sake tabbatar min. But I cannot marry you" Ya koma da baya har sai da ya jingina da jikin kujera sannan ya zauna. Emotions dinsa mixed up. "Why?" Ya tambaya at last. Na fara kuka "saboda Daddy yace in rabu da kai. Yace ba zai aura min kai ba. Ya kuma ce ko bayan ransa bai yarda in aure ka ba. Ba zan iya bujirewa maganar sa ba. He went through a lot a kaina, Ina so nima in faranta masa rai in yi masa biyayya ko da kuwa hakan yana nufin zan rasa abu mafi soyuwa a gare ni. Dan Allah Muhammad kayi hakuri...…”. Sai ya dafa kujera ya mike bai ce min komai ba, sai kuma jiri ya debe shi ya tafi zai fada kan kujura, na tafi gurinsa da sauri kamar zan rike shi sai ya daga mun hannu amma sai ya zauna akan kujerar, Na cigaba da kokarin yi masa magana Gidado, Iyayen mu sun fi koma muhimmanci a gare mu. Mama da Abba ba sa so. Daddy baya so. Both our families ba sa so. Soyayyar da muke yiwa junan mu is not enough especially in zata bata musu rai dan farin cilkin su yafi namu muhimmanci. Dan Allah ka fahimta." Ya dago kansa ya dafe da hannun sa yace "are you telling me inje in cigaba da zama da Safina kenan? Makaryaciya, mayaudariya munafuka? Ita kike so in zauna da ita ta haifa min yaya? And you? Who are you going to marry? Ko akwai wani ne dama da ban sani ba? Na girgiza kaina tare da kneeling down a gabansa. “Babu kowa Muhammadu. Babu kowa a zuciya ta sai kai. Nima ban san wanda zan aura ba. Na yanke hukuncin zan bawa Daddy zabi ne kawai, duk wanda yaga ya dace sai ya aura min in dai hakan zai saka shi farin ciki. Dan Allah kai ma kayi haka. Ka bawa su Abba zabi”. Ya mike tare da daukan key din sa sai na mike na kwace "dan Allah kar kayi fushi da ni Muhammad, It hurts me a lot to make this decision amma dole ne. Kai ne farin ciki na, amma farin cikin Daddy yafi nawa muhimmanci a gare ni. Dan Allah Muhammad kayi hakurj" ya miko min hannu, still expression dinsa unreadable '"bani key dina" na matsa baya ina girgiza kai "ba zan barka kayi driving a wannan yanayin ba" cikin fada yace "you don't care. Don't pretend that you do" nace "but I do, more than you know" ya tako ya dawo gaba na ya tsaya yace "do you truly love me?" Na gyada kai na da sauri "fiye da yadda kake tunani" sai yace "then I will not give up. Ke kiyi abinda kike tunanin shine dai dai, nima zanyi abinda nake tunanin shine dai dai. Kamar yadda nace, soyayyar ki kaddara ta ce, then there is no turning back". Ya juya ya sake yin hanyar fita nace "key din ka yana hannuna, I will not let you drive" yace "ki rike. Zan shiga ta haya". Daga haka ya fita. Na koma na zauna akan kujera tare da dafe kaina ita share sauran hawayen fuska ta sai kuma na mike da sauri na bi bayansa, Sanda na hango shi har ya kusa kai wa bakin gate,. Tun daga tafiyar sa ma zaka gane cewa hankalin sa ba'a tare da shi yake ba, na ga Malam Ya'u ya bude masa kofa yana bin sa da kallo har ya fita ya rufe kofar sannan ya juyo muka hada ido, ya jima yana kallona nima sai kuma ya koma gurin zamansa ya zauna. Na sauke ajjiyar zuciya sannan na juya zuwa cikin gida cikin sauri mai hade da sassarfa. Na san next stop din Malam Ya'u shine gurin Daddy, a matsayin sa na loyal maaikacin Daddy da ya dauki shekara da shekaru suna tare, yana taya shi looking out for his family ne a lokacin da shi Daddyn yake kwance babu lafiya. Ni kuma haka nake so dama. Ina sane na bar shi ya ga komai. Babu kowa a parlour saboda an fara kiraye kirayen sallar magrib dan haka na wuce sama zuwa dakina na shiga na rufe kofa. A bakin gado na zauna tare da dafe kaina ina kokarin bitar maganganun mu da Muhammad amma na kasa saboda kaina gabaki daya ya toshe ya cunkushe. Hankali na gabakidaya yana kansa, Fatan kawai da nake yi shine ya fahimci message din da na tura masa, ya fahimci ba da gaske nake ba cewar da nayi ba zan aure shi ba, Na je window na bude labule amma bana iya hango shi. Ko ya samu abin hawa? Na hango Baba Ya'u a bakin gate yana alwala, na danyi murmushi kadan, na san yana yin sallah zai tafi gurin Daddy ya kai rahoton zuwan Muhammad kuma ya gaya masa inda muka zauna ni da shi. Ina sane nake barinsa yana ganin mu, ina sane kuma na zabi inda zamu hadu da Muhammad din dan ina so Baba Ya'u ya ga shigar mu. Dan ina so ya gaya wa Daddy exactly inda muka zauna. Na fahimci cewa it took Daddy long to see maganganun mu da Mustapha saboda cameras din suna da yawa shi kuma bashi da isasshen lokaci, kuma bai san wacce Camerar zai duba ya samu wani abun kirki ba. Yanzu kuwa Baba Ya'u zai gaya masa exact camera din da zai duba da kuma exact time din da muka zauna. And he will see and hear everything. And then he will know gaskiya akan komai da komai. Ni kuma nawa yanxu shine inyi folding arms dina in jira matakin da zai dauka. Na koma bakin gado ina shafa idanuna da suka kumbura saboda kukan da na sha yau, na dauki wayata na gwada number din Muhammad amma har ta gama ringing dinta bai dauka ba. Na sake jin hankali na ya tashi a kansa, na kara kira still shiru sai na tura mass text "Baby please call me as soon as you see this. I need to explain things" Na dan jira kadan sai kuma na tashi na shiga toilet nayi alwala ina gaya wa kaina maybe shima ya tsaya sallah ne ko kuma har yanzu yana hanya. Sai da na idar da sallah na gama adduoi na sannan na sake daukan wayar na duba amma babu call dinsa kuma bai yi replying message dina ba. A lokacin iya kololuwar tashin hankali na shige ta, na zauna akan gado na dafe kaina "ya Rabbi" na ambata a hankali. Kamar daga sama naji ana buga kofar dakina, na tashi na bude na ga Hassan a tsaye yana kallona yace "Yaya ki zo inji Daddy" sai da naji kamar dan karamin fitsari zai fito, na dafe kofa ina kallon Hassan da shima yake kallona da alamar tambaya yace "are you okay" na gyada masa kai da sauri sannan na koma cikin dakin tare da rufe kofar na jingina da jikinta. Hankali na duk ya rabu gida biyu, ban yi tsammanin samun kira daga Daddy yanzu ba, sannan kuma ina tunanin halin da Muhammad yake ciki. Sai da na shiga toilet na dan watsa wa fuska ta ruwa duk kuwa da cewa babu abinda tayi sannan na fita da waya ta a hannu still expecting a call from Muhammad, Ina zuwa zan shiga part din Daddy muka hadu da Baba Ya'u yana fitowa, Ya bani hanya na wuce sannan ya bini da kallo. Sai na sauke ajjiyar zuciya tare da bismillah sannan nayi sallama na shiga, Yana zaune akan kujerar sa. Kallo daya zaka yi masa kasan yana cikin damuwa mai yawa. Na zauna a kasa ina addu'ar wannan damuwar da zan saka shi a ciki ta zama ta karshe, nace "Daddy ganj" ya kalle ni ya dauke kai, kamar ba zaiyi magana ba sai kuma yace "waye yazo gurin ki da zu?" Nayi shiru bance komai ba. Ya sake cewa cikin karyewar murya "ba kya jin magana Safiyya. Me yasa ba kya jin magana ne wai? Yanzu idan Sa'adatu ta ga mijin Safina yazo gurin ki zance kina ganin zata ji dadi?" Nace "Daddy kayi hakuri, na kira shi ne na gaya masa abinda kace. Na gaya masa ba zan aure shi ba. Ba zan kara bata maka rai ba insha Allah Daddy. Duk abinda ka ce shi zany" yayi shiru yana studying dina sannan ya sake cewa "me motarsa take yi a gidan?" Nace "he couldn't drive after I told him that. Shine ya bar ta anan. Zai aiko a dauka" Daddy yay dan murmushi ace "lies........ He wants you to believe that. He wants you to think he care" nayi shiru ban ce komai ba sai ya ce "ki dauko key din motar Ki bayar a kai Bana son yayi amfani da wani uzuri ya sake dawowa gurin kj" na gyada kai sannan na mike zan fita yace "Safiyya" na juyo yace "you did good. Allah yayi miki albarka" a hankali nace "'Ameen ya Rabbi". Sama na koma na dauko key din, ban sauko ba sai da na sake kiran number din Muhammad, amma yanzu bata ma shiga, na sauka da key din na bawa one of my guards na bashi address din da zai kai. Duk zirga-zirgar da nake yi Mommy tana parlour tana kallona bata ce min komai ba kuma bata tambaye ni komai ba. Dama yanzu ta ja baya sosai da yi min magana tun akan issue din Mustapha, a fahimta ta kamar tana zargin ina da hannu akan korar Mustapha da Daddy yayi dan a rushe maganar auren mu. Ban zauna a parlourn ba sai na koma dakina. Na zauna akan kujera ina jujjuya wayata hankali na a tashe. Nayi ajjiyar zuciya tare da lumshe ido na ina bitar maganganun mu da Muhammad. Tabbas maganar da ya fada min akan Safina ta taba zuciya ta sosai, fiye da yadda nayi tunanin zata taba ni din. All my life ba zan iya tuna wani abu da nayi mata da nayi deserving abinda tayi min ba. At least ta gaya masa gaskiya mana? Ko da gaskiyar ta gaya masa ba ta kyauta min ba ballantana wanna irin karya haka. Wato ita duk halin da na shiga da abin da ya same ni bata ji tausayi na ba ma sam, maybe ma murna tayi da faruwar komai, Nayi tunanin labarin da ya bani na yadda taje social media tana cigiyar sa. Yace Mufida tace kusan shekaru biyu da suka wuce ne. Lokacin ma muna tare da Muhammad, lokacin muna tsakiya da kafa soyayyar mu, wato tun a lokacin tayi niyyar raba mu, kamar yadda Muhammad ya fada zata iya yiwuwa tun a lokacin ta dauki number dinsa a waya ta ta kira shi tayi masa tayin soyayyar ta yayi rejecting shi kuma, Shi yasa ta cigaba da yi min bincike with any opportunity da ta samu, looking for something that will link her to him. Na sake kiran number din Muhammad, still a kashe, ji nake yi a kamar in zauna inyi ta kuka. Sosai nake so inji muryarsa. So nake inyi masa bayanin plan dina da kumaoutcome din da nake saka rai. So nake in kwantar masa da hankali in kuma jaddada masa soyayyar sa da take cike a zuciya ta.[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: Na sake kiran number din Muhammad, still a kashe, ji nake yi a kamar in zauna inyi ta kuka. Sosai nake so inji muryarsa. So nake inyi masa bayanin plan dina da kumaoutcome din da nake saka rai. So nake in kwantar masa da hankali in kuma jaddada masa soyayyar sa da take cike a zuciya ta. Him👳🏻‍♀️ The last few weeks have been a rollercoaster of emotions for him. Daga wancan sai wancan sai wancan., And abubuwan ba Wai suna zuwa ne one after the other ba, suna zuwa ne wani issue din a cikin wani kuma har yanzu babu wanda ya samu yayi solving, dan duk issues din are linked to one thing, to one person, Safiyya. Bai gama warkewa daga shock din karairayin da Safina ta gaya masa ba, wadanda ya san cewa Karya ce amma kuma still akwai something in them da yake son jin gaskiyar sa daga bakin Safiyya, Sai dai sanda ya samu Safiyya kuma har tayi alkawarth fada masa gaskiyar komai akan ta sai ta fara da labarin mahaifiyar ta da yadda ta rasa kowa nata. Labarin ya tabashi sosai ya kuma saka masa tausayin Safiyyan a cikin zuciyar sa, knowing bata da kowa a bangaren uwa. And then a zaman su na biyu sai ta bashi labarin da yafi wancan ruguza tunanin sa, labarin kasan cewar ta mai kudi fiye da tunanin sa. A Daren kusan kwana yayi bai yi bacci ba yana jujjuya maganar a cikin kansa wannan wani abu ne dabai taba tunani ba. A matsayin sa na namiji, plans dinsa was always been to be a provider to his family, to work hard and take care of his wife and kids and treat them like queen,princes and princesses kamar yadda yaga Abban sa yana yi, amma yanzu knowing Safiyya bata ma cikin class dinsa a kudi sai abin yazo masa bazata, shi bamai kudi bane ba. Iyayen sa dai suna da kudi amma yanzu ne kokarin kafa roots dinsa da tallafin iyayen na sa. Amma soyayyar da yake mata sai ta saka ya hadiye wannan fear din, ya rarrashi kansa da cewa tana son shi kuma ba zata ke raina abinda zai ke providing mata ba, hakan kuma sai ya kara masa zeal din doubling efforts dinsa na neman kudi to meet up with her. Amma kuma a ransa ya son Cewa Wannan maganar ba ita ce wadda yake anticipation din ba, yasan cewa the worst is yet to come. Duk da zullumin da zuciyar sa take ciki hakan bai hana shi cigaba da gaya mata yana son suyi maganar ba, dan yasan dole sai sunyi sannan sannan zasu samu fahimtar juna. A gefe daya kuma ga issue din Safina da ta zame masa karfen kafa, dan yanzu ma tana gidan su tana cigaba da jinya acan tunda taki tafiya gidan su, ko kuma yace gidan su Safiyya. Su kuma iyayenta sunyi fushi sun kwashe mata masu kula da ita. A daya bangaren kuma ga iyayensa da har yanzu suke fushi da shi akan dukan Safina da yayi, da kuma soyayya da suka san cewa yanayi da kanwar matar sa, Yayi yayi su bashi damar yi musu bayani amma sunki, su a nasu ganin wannan fushin da suke yi da shi shine punishment dinsa kuma shi zai saka ya dawo cikin hayyacin sa ya fahimci abínda yake yi ba dai dai bane ba. Su a ganin su Safiyya ta kashe auren ta ne dan ta ga ya auri yayarta, shine ta dawo ba wai dan tana son sa ba sai don ta kashe masa aure, and they fear she will break his heart again. Wannan yasa duk kokarin bayanin da yake yi musu ba sa ganewa, su a gurin su blind love yake yiwa Safiyya dan haka baya gane aibun ta baya ganin laifinta sam. Dan breakthrough din da ya samu kawai shine kasancewar Mama yanzu ta gane Safina makaryaciya ce, kuma ranta ya kara baci akan hakan sanda Safina tayi masa sharrin kade ta da mota, in fact yanzu ya fahimci Mama tana yiwa Safina abubuwa ne kawai out of the goodness of her heart kuma saboda matsayin matar sa da take dashi amma ba Wai dan tana son ta kamar da ba. And a ransa yasa cewa ta wannan bangaren ne zai samu waraka daga wannan virus din mai suna Safina da ya dabaibaye shi, And then one day Safiyya called him to their house tace zasu yi maganar da yake ta dreading, Tun kafin yaje gabansa yake faduwa, ya tabbatar zai ji abubuwan da zasu taba masa zuciya har bama ya son yayi hasashen abinda zai ji din, but he tried to get as ready as he can, Ya shirya gaya mata dukkan gaskiyar sa, ya kuma yi fatan itama zata gaya masa ba tare da ta boye wani abu ba, Sai dal yana packing a cikin gidan nasu ya ga sakon ta, wai zata gaya masa gaskiyar komal amma kuma maganar ta ta karshe ba gaskiya bace ba, And that destabilized him, Wacece maganar karshe din? And why? Amma bai ga fuska da space din tambayar ta ba, ita ma ya ga tsoro da tashin hankali a fuskar ta sanda ta fito, and more than anything, ya ga soyayyar sa. Wannan kuma shine zaren da yake rike da hope dinsa, as long as yana ganin soyayyar sa a cikin idonta, he will never give up They talked, he told her everything kamar yadida yayi wa kansa alkawari, maganar karshe akan abinda Safina ta fada a kanta ta taba ta sosai har sai da yay nadamar gaya mata, wannan kuma ya sake tabbatar masa da cewa Safina karya take yi. But then kamar yadda yayi tunani, there is something there, Wannan something din kuma shine abinda yayi finding out when she told him her own side of the story. She was raped. And kuma a yanzu haka tana da da, alive and healthy. Wanna labarin is one of the worst news da Muhammad ya taba samu a rayuwar sa ta duniya. But what was more terrifying is what she went through. Shi bai tana jin wannan tashin hankalin ba. She went through hell on earth ba tare kuma da tayi laifin komai ba. And she went through it alone, And she went through part of that to protect him from taking blame for something he didn't do. Wanna labarin ya ruguza dukkan tunanin sa, ya rusa dukkan katangar da ya zagaye emotions dinsa da ita and he cried with her. Sai dai kuma labarin ya kara masa soyayyar ta a cikin zuciyarsa, if that is possible, dan dama zuciyar a cike take da soyayyar ta ta. Ya kuma kara fahimtar kyawun zuciyar ta da har ta iya rabuwa da Mukhtar yake cigaba da yawo freely a gari. Ya dauki aniyar sai Mukhtar ya yi nadamar abinda yayi mata, ita kuma tayi kokarin dakatar da shi kuma ya dakata din amma kuma ba wai ya bar maganar bane ba, ya tsaya ne dan su samu damar kammala maganar su, su kuma samu damar rarrashin juna. Hakan kuwa suka yi. After re-pledging their eternal love for each other, sai ya sake tabbatar mata da kudirin sa na son auren ta but to his biggest surprise sai tayi rejecting, tace wannan ita ce last maganar da zasuyi. Ta kuma ce rabuwa ma zata yi dashi dan yin biyayya ga mahaifinta. Wannan maganar tata ce ta saka ya tuna da sakon da ta tura masa kafin ta fito wajensa, and a take ya fahimci abinda yake faruwa, someone was watching them, probably Daddy, Wannan tunanin ya kara daga masa hankali, yaji babu abinda yake so irin ya fita daga wajen tun kafin kansa ya buga sabada rudanin da yake ciki, amma sai ta karbe key dinsa ta cigaba da kokarin gayawa wanda yake jin su cewa she was breaking up with him. He told her tayi abinda take ganin dai dai ne shima zai yi abinda yake ganin dai dai ne. Sanda ya fito daga gidan jiri ne kawai yake diban sa, maganganu ne kawai suke overlapping a cikin kansa ya ma rasa wacce zai dauka yayi tunani akai. Wani bangaren a zuciyarsa haushin Safiyya yake ji, me yasa ba zata gaya masa cewa wani yana jin su ba? Haushin kowa ma yake j, including shi kansa. Tabbas, soyayyar Safiyya ita ce babbar jarabawar sa a rayuwa. Taxi ya samu ya shiga sannan ya bawa driver din address din gidan sa, gidan da ya gina da sunan Safiyya, shi yasan ba zai iya zuwa gida a cikin wanna halin da yake ciki ba, dan kallo daya Mama zata yi masa ta saka shi a gaba da tambayar me ya same shi, daga ya ambaci sunan Safiyya kuwa shikenan lamari ya lalace dan zata iya cewa ma Safiyya ta lashe mata kurwar da. Plus in yaga Safina a yanzu zai iya shaketa har sai ta daina numfashi. Gidan nashi aka kai shi kamar yadda ya bukata, sai dai shi kansa drivern ya fahimci ba'a cikin hayyacin sa yake ba, ya tambaye shi ko bashi da lafiya amma bai amsa masa ba, Da kyar ya dauko kudi ya sallami driver din sannan ya juya cikin hada hanya ya karasa gate yay knocking. Mai gadi da yake shirin tafiya masallaci ya bude, sannan ya tsaya yana kallon sa cikin damuwa "ranka ya dade baka da lafiya ne? Ko jikin ne?" Bai amsa masa ba shima ya wuce shi yayi hanyar shiga cikin gidan, sai dai kafin ya karasa kofa ya yanke jiki ya fadi a gurin, Mai gadin ya karaso kansa da sauri yana girgiza shi tare da karanto duk adduoin da suka zo bakin sa. Sama sama Muhammad yake jinsa, ya fara kokarin sake tashi amma sai yaga kamar mai gadin ya zama mutum hudu duk masu kama daya, ma'ana hudu hudu yake gani, ya tabbatar kuma yana sake tashi faduwa zai yi. Ya tuno da maganar Piya ranar da ya taho gidan da niyyar zai kwana shi kadai "in wani abun ya same ka fa?" Ya mayar da idonsa ya rufe sannan ya cewa mal gadin "kirawo min Abba na"., A cikin kan sa yaji wayarsa tana ringing da kidan da ya sakawa Safiyya. Bai fito da wayar ba ma ballantana ya dauka Ya tuno maganar da ya gaya mata ta karshe, tayi abinda take ganin dai dal ne shima zai yi abinda yake ganin dai dai ne. She definitely had a talk with him and Daddy at the same time, shima yanzu he is going to have a talk with Abba. Yana jin mai gadin ya gama waya da Abba yana gaya masa halin da yake ciki, sai ya fara kokarin mikewa mai gadin ya taimaka masa, sannan ya bude masa daki mafi kusa da su ya saka shi a ciki. Babu komai a dakin sai carpet, akan carpet din Muhammad ya kwanta tare da rufe idonsa, yaji Safiyya ta sake kiran sa amma bai dauka ba, Ba wai fushi yake yi da ita ba, amma dai baya son yin magana da ita a yanzu, baya son yin magana da kowa. Sai da kiran ya katse sannan ya jawo wayar ya kashe ta ya ajiye a gefe, ya cigaba da kwanciya yana sauraron yadda kansa yake sarawa da karfi kamar zai tsage. Abba ya fito daga masallaci zai shiga gida kenan mai gadin ya kira shi. Daga yadda yaji muryarsa ya san babu lafiya, sai ya gaya masa Muhammad ne gashi ya je gidan kuma kamar bashi da lafiya ya kuma ce a kira sama shi. Wannan ya saka ya fasa shiga gidan sai dai bai gayawa haidar dalili ba dan yasan halin Maman su in dai akan yaya ne yanzu zata tayar da hankalin ta. Sal ya ce masa kawal zai je wani guri ya dawo. Sal dai yana kokarin shiga motar sane yaga shigowar motar Muhammad gidan, amma maimakon ya ga Muhammad din ya fito sal ya ga wani wanda bai sani ba, wani mai kama da kuma shiga irin da security officers, Har ya fara tunanin ko wani laifi Muhammad din yayi sai mutumin ya gaishe shi ya ba shi key din motar yace "from my boss, Safiyya Adam, tace a kawo wa Muhammad na gidan nan motarsa, ya barta a gidan su sanda ya je" Abba ya karbi key din yana maimaita wa "boss? Safiyya Adam? Gidan su?" Amma security din bai amsa ba kuma Abba ya san ba zai amsa ba, haka training din su yake, abinda aka saka su shi kadai suke yi basa interfering ko asking ko answering personal questions. Sai kawai ya saka key din a aljihu ya shiga motar sa ya tafi inda Muhammad din yake. Tabbas, ya san komai ba ake ciki dangane da matsayin Safiyya tsohuwar budurwar Muhammad a gurin Safina matar Muhammad. Tun daga sanda ya san hakan sai ya fahimci cewa trouble dey Muhammad yana kwance yaji shigowar Abba, Ya bude idonsa kadan sai yayi sauri ya mayar da shi ya rufe saboda jiri da yaji ya cigaba da fiban sa duk kuwa da cewa a kwance yake. Abba ya durkusa a gabansa tare da dora hanunsa akan goshinsa da kuwa wuyan sa. Sai kuma ya mike ya dauko wayarsa ya kira likitan su ya fada masa inda zai zo ya same su. Daga nan ya saka mai gadi ya dauko wa Muhammad din katifa da kayan shinfida a cikin gidan yazo ya saka masa anan dakin, yayin da shi kuma ya taimaka masa yayi alwala yayi sallah sannan ya kwanta a dai dai lokacin da Dr ya shigo. Duba shi yayi, a take yayi concluding "bp dinsa yayi sama gaskiya. We will have to watch it kar ya zame masa matsala" Abba ya runtse ido cikin jin zafin maganar, ko shi ba shi da hawan jini ballantana dan jaririn dan sa. Dr ya gama duba shi ya fita ya siyo duk abinda yake bukata sannan yazo ya daura masa ruwa yayi masa allurai a cikin ruwan sai yayi wa Abba sallama ya ce sai da safe zai dawo ya sake duba shi. Bayan ya fita Abba ya zauna a kusa da kan Muhammad yana kallon yadda gumi yake karyo masa alamar zazzabin da ya rufe shi ya sauka, ya shafa kansa a hankali tare da kiran sunan sa “Gidado….. ko zamu koma gida ka kwanta a can?” Muhammad yadan bude idonsa kadan ya kalle shi sannan ya girgiza kansa yace “no Abba. Anan zan zauna. Bana son zuwa gida” cikin kokarin bugar cikin sa Abba yace “ saboda me” Gidado yace “mama zata tayar da hankalin ta in taga bani da lafiya. Kuma bana son ganin Safina” Abba ya sauke ajiyar zuciya yana cigaba da kallon fuskar Muhammad, daga yadda fatar idonsa ta kumbura ya san yayi kuka, shi ba zai iya tuna rabon da yaga dan nasa yayi kuka ba, wannan kuma yakara tayar masa da hankali, ya sake tambayar sa “daga ina kake? me ya same ka?” Muhammad yasake bude idonsa, tambayar dayake so yayi masa kenan, tambayar daya sa aka kira masa shi dan yayi masa kenan, dan haka direct ya bashi amsa “daga gidan su Safiyya……. We broke up again……. Daddyn ta yace ba zai aura mata ni ba. Kuma kunce ba zan aure ta ba”. Daga haka ya juya wa Abba baya, ya gama maganar sa saura ya jira amsa daga mahalfinsa, kamar yadda Safiyya itama ta gama tata maganar take jiran amsa daga nata mahaifin. Maman Maama ✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Fifty Eight: Parenthood Not Edited Abba ya sauke ajiyar zuciya yana kalion sa, shi bai san a inda yaron nan ya koyo taurin kai ba, yaro ne shi mai biyayya, ba'a taba ce masa yes yace no ba. Amma yanzu yana nema ya birkice musu. Yasan duk abinda suke ciki amma bai yi magana a kai ba saboda ya fi son ya san komai a kan maganar first kafin yayi magana, yadda in yace no zata tsaya a no din haka zalika in yace yes. Amma kuma duk da haka already shi da mama sun san abinda dan nasu ya ke so abu ne mai wahalar tabbatuwa, bayan kasancewar yarinyar nan step sister din matarsa akwai abubuwa da yawa da suke cukurkude a cikin lamarin yarinyar wadanda suke bukatar warwarewa. Misali dazu wani katon mutun mai fuskar marasa mani yazo ya kawo masa key din motar Muhammad kuma yace inji boss din sa sannan ya ambaci sunan safiyyan as boss din nasa, How? But high bp? Muhammad? Saboda sun rabu? Ko kuma yace saboda sun ce zasu rabu dan yadda yake ganin dan nasa da kuma yadda yayi masa magana bai nuna alamar da gaske zai rabu da yarinyar ba. Meaning high bp yanzu ya fara shi kenan. Ya sake saka hannun sa a wuyansa da goshin sa yana jin yadda jikinsa yake kara yin sanyi sannan ya mike tsaye yana kallon sa tare da sauke ajjiyar zuciya, ya san ba bacci yake vi ba, wannan juya masa bayan da yayi ma'ana fushi yake yi da shi kenan, fushi yake yi da su shi da maman sa dan sun hana shi abinda suke ganin cutarwa ne a gare shi. A hankali yayi magana "zan koma gida Muhammad. Kar maman ka taji ban shigo ba ta fara damuwa and bana son ta san baka da lafiya, bana son ta san kana neman dora wa kanka ciwon da Allah bai dora maka ba. I will discuss it with her a hankali. Ka kwantar da hankalin ka, zan saka ayi min bincike akan yarinyar, in ta kama zan je har gidan su inga mahaifinta inji in yana da masaniya akan abinda yake faruwa or not", Muhammad bai ce komai ba amma Abba ya san ya jishi. Sai ya juya ya bar gidan bayan ya gaya wa mai gadi yayi keeping eye on Muhammad din kafin ya dawo ko ya aiko a dauke shi. A hanya ma maganar yake ta juyawa a ransa, shi bai san wannan wacce irin yarinya ba ce ba mai shegen nacin da ta ki bar masa zuciyar da ta huta, bai san kuma dalilin da shima Muhammad ya nace mata ba kamar babu sauran mata a duniya. Shi ya san dan sa da farin jinin yammata kamar yadda shima yayi a lokacin samartakar sa, shi da kansa da yake namiji iyaye a family sun sha yi masa tayin a hada Muhammad din da yayansu dan a kara karfin zumunci, Mama ma haka ta kan samu daga gurin yan'uwa da kawaye, shima kuma Muhammad din duk da baya fada amma sun san yammatan suna cire kunyarsu at times suyi mass tayin soyayyar su, hakan yana nufin idan guda hudu yake so to tabbas zai samu da gudu, but why her? Why this Safiyya? Mama ta gaya masa cewa yarinyar tana da kyau amma wannan kadai bai isa dalilin makale mata ba, dan ya tabbatar ba za'a ce tafi kowa kyau ba. Amma dole zasu zauna akan issue din nan shi da Zainab, dole zasu samarwa dan nasu mafita akan maganar nan tun kafin tayi masa Illawarra da baza su iya magance masa ba. Amma hakan baya nufin zasu tunkuda shi ga halaka dan su faranta masa, idan Safiyya ba yarinyar kirki bace ba kamar yadda suke tsammani hada ta da dan su da yake yaron kirki ba. Ba zasu bari ta karasa kashe musu shi ba. Ya shiga gida yayi packing ya fito yana kalion motar Muhammad din, a ransa ya danyi tunanin maybe a new car will cheer him up tunda dama yaje ya lalata waccan saura wannan. Ya shiga cikin gidan, Mama bata parlour, wannan ya bashi mamaki dan ya san yanzu lokacin zamanta ne a parlour har sai duk sunci abincin dare ta tabbatar kowa baya bukatar komai sannan zata koma ciki, Ya zauna yana kallon hanyar dakin da matar Muhammad take ciki tana jinya, jinyar ciwon da tace shi yaji mata amma kuma bincike ya tabbatar musu ba da sanin sa bane ba, in fact zai iya cewa yarinyar ce ta jawo faruwar abin. But Muhammad ya mare ta, wannan shi da kansa bai musa hakan ba. Wannan ya sa dole suke tausayawa yarinyar duk kuwa da sharrin da ta nemi makalawa dan na su, abinda suka sani thine matar Muhammad ce kuma tana son sa sosal da sosai, and she carried their grandchild for a while kafin su rasa phi. Sun kuma san cewa ba karamin takaici Muhammad yake cusa mata ba a cikin auren su musamman yadda yake soyayya da step sister din ta. Wannan kuma shine gurin da Abba ya sake diga ayar tambaya. How? Ta yaya suka zama step sisters? Ta yaya kuma babu wanda ya san step sisters din ne sai yanzu? Ya sake mikewa ganin har yanzu Zainab bata fito ba ballantana ta bashi abinci kamar yadda ta saba. Yana son kuma suyi wannan maganar da ita. Yana son ya samu amsar da zai bawa Muhammad dan ya kwantar masa da hankali. A lokacin Haidar ya shigo, shima ya fara baza ido a parlour daga dukkan alamu mahaifiyar ta sa yake nema shima. Sai kuma yace da Abba "Abba barka da dawowa. Ina Mama?" Abba yace "yanzu na shigo. Bata fito ba tun dazu?" Haidar yace "tun sanda na shigo na ga ta fito daga dakin Safina sai kuma ta shiga ciki, ina jin dakin ta ta tafi, na gaji da jiran ta na sake fita sai yanzu na dawo". Ba tare da Abba yace masa komai ba ya tafi dakin nata, zuciyar sa tana gaya masa something is wrong with her, dan babu yadda za'a yi la shiga daki ta zauna ita kadai a wannan lokacin. Shi ya dauka ma tana nan ta ishi kowa da tambayar ina ya tafi? Kuma ina Muhammad? Ya tura kofar dakin nata a hankali yana jin sanyi da kamshin dakin, sai kuma ya tsaya a bakin kofar yana kalion ta a zaune akan gado da wayarta a hannun ta fuskarta a kasa. Ya tabbatar taji shigowar sa amma bata dago kai ta kalle shi ba, damuwar sa ta kara yawa, dalili biyu ne zai saka tayi haka, ko dai yayi mata laiti tana fushi da shi ko kuma kuka take yi bata son ya gani. Ya karasa shiga dakin tare da rufe kofar, sannan ya taka a hankali zuwa gabanta ya tsaya, sai ya ga ta kara boye fuskarta tare da saka hannunta tana goge fuskar, wannan ya tabbatar masa da cewa kuka take, hawayen take share wa. Wannan kuma ya tayar da hankalin sa sosai. Ya durkusa a gaban ta tare da saka hannu ya juyo fuskarta gare shi. Ta kale shi din kamar yadda ya bukata, idonsa ya sauka akan nata da suke nuna alamun kuka duk kuwa da cewa ta goge hawayen. Ya mayar da idonsa kan cinyarta ya ga wayarta a ajjiye, wannan ya tabbatar masa da cewa koma menene ya saka ta kukan a waya aka gaya mata shi. "Waye ya mutu?" Tambayar da ya fara yi mata kenan cikin fulatanci. Tayi saurin girgiza kanta tare da yin gyaran murya kadan tace "babu wanda ya mutu. Sannu da zuwa" ya mike tsaye sannan ya zauna a kan gadon kusa da ita yace "menene ya saka maman Muhammad kuka?" Ta dan yi murmushi, babu halin da zata shiga a ambaci dan nata ba tate da ta murmusa ba. Duk da cewa a kwanakin nan shine silar shigarta damuwa sosai. Wannan kukan ma nasa ne. Ta dalilin sa ne. Ya saka hannu ya dauki wayar tata yace "bara in gani, waye ya saka min matata kuka? Tabbas zan dauki mataki akan ko waye, sai inda karfi na ya kare" ta sake yin wani murmushi wanda yafi wancan girma sannan ta saka dan yatsa ta dauke hawayen da ya sake makalewa a gefen idonta. "Hajjo" taji ya ambata a hankali yana danna wayar ta, sannan ya sake cewa "allai tafiya Germany ta same ni kenan. Sai naje naji me Hajjo ta gaya wa matata da ya saka ta zubda hawaye. Let me quickly get flight tickets" ta kamo hannun sa tana cigaba da murmushi tare da kwantar da kanta a kafadarsa tace "in ka tambayi matar ta ka zata gaya maka ai, ba sai ka sha wahalar neman bayani ba" yace "gwara dai in tafi neman bayanin, dan a gane girman damuwata" sai kuma ya kara da tambayar "me ya faru?" Ta dago kai tana kalion sa, annurin fuskarta yana gushewa, ta kuma tina da alkawarin da tayi wa Hajjo yanzu a waya, sai ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace "ina so zamuyi magana, akan Gidado, akan yarinyar da yake so Safiyya. Amma muje ka fara cin abinci tukunna" ya kalle ta da mamaki "Safiyya? Nima da shirin yi miki magana akan ta na shigo. Me ya faru?" Ta mike tsaye tare da kama hannun sa tana kokarin dawo da annurin fuskarta tace "muje muci abinci tukunna. Kar Haidar yaji mu shiru ya damu. Ina Muhammad?" Tayi tambayar da dama ya tabbatar zata yi masa, sai ya mike yana cewa "ya kira ni yace akwai abinda ya rike shi sai anjima zai dawo gida". Daga haka suka juya suka fita tare. Cin abincin nasu ya kasance cikin shiru, kowa yana juya maganganu da yawa a ransa har suka gama. Haidar kan sa ya fahimci akwai wani abu da yake damn iyayen nasa, yayi kokarin ya ga sun saki ransu kamar kullum amma ganin hakan yaki yiyuwa sai ya bar maganar shima kawai yaci abincin sa, Sai da suka gama sannan Abba ya danyi gyaran murya yace wa Haidar din "kaje gidan Gidado na........... Yana can a kwance bashi da lafiya. Idan ruwan da aka saka masa ya kare sai ka taho dashi ku dawo gida" "bashi da lafiya?" Mama ta fada tana zaro ido, Abba ya daga kafada "dana gaya miki da ba zaki ci abinci ba. Duk da yanzun ma ba sosai kika ci ba. Bashi da lafiya but he will be okay" Haidar ya mike amma shima yana jin babu dadi a ransa, yayan na sa yana ta shiga damuwa iri iri a kwanakin nan, Daga nan basu sake maganar ba sai ya mike ya tafi gabatar da sallar ishar da ya rasa ta a jam'i lokacin yana hanyar dawowa daga gidan Muhammad, ita kuma ta kira ma'aikatan gidan suka fara hidimar gyaran gurin sannan ta shiga sauran hidimomin da ta saba yi duk dare a gidan dan tabbatar da komai is in order. Sai da ta gama sannan ta tsaya tana kallon dakin da Safina take ciki tana jin wani iri a zuciyar ta, ba zata iya shiga dakin ba yau kamar yadda ta saba shiga kullum da dare kafin ta kwanta. Sai ta juya tana kallon yar aikin ta mai suna A'isha wadda yanzu ita take taya Safina kwana, tace "A'isha shiga ki tambayi Safina in akwai abinda take bukata, kin kai mata abinci taci?" A'isha tace "na kai mata abinci tun dazu, amma bara in koma in tambaye ta ko tana son wan abu" Ta shiga dakin, bata jima ba ta fito yanayin fuskarta babu dadi, hannun ta dauke da tray din abinci ta ajiye shi akan cabinet din kitchen din tace "bata ci abincin ba Mama. Kuma tace min bata bukatar komai" Mama ta cigaba da kallon ta fuskarta da alamar tambaya amma bata yi tambayar ba sai A'isha ta amsa "kuka na tarar ta na yi. Maybe ko hannun ne yake yi mata civo" Mama ta gyada kai tace "maybe" sai kuma ta cigaba da al'amuran gaban ta. Sai data gama ta shiga dakin ta ta cire kayanta tayi wanka tare da alwala tazo tayi sallar shafa"i, bata yi wutiri ba dan tana da niyyar tashi cikin dare tayi sallah kamar kullum, sai ta dauko Alqur'anin ta ta fara karatun suratul mulk kamar yadda take yi duk dare kafin ta kwanta. A lokacin ne yayi sallama ya turo kofar a hankali, jin karatun ta ne ya saka ya karasa shigowa tunda ya tabbatar a suturce take sai ya zauna acan gefe yana kallon ta. Bata dago kai ba duk kuwa da zuciyar ta tana son gain sa musamman tunda an gaya mata bashi da lafiya. Haka suke yi yanzu, tunda aka sallamo shi daga asibiti take yin fushi da shi akan laifin dukan matarsa da yayi, amma kuma zuciyarta tana matukar tausaya masa halin kuncin da tasa zuciyar take ciki kuma tana neman hanya mai kyaun da zata bi ta saka dan lelen nata a farin ciki in dai hanyar ba haramun bace ba kuma ba zata cutar da shi in the future ba. Sai dai ta cigaba da tsare gida ne dan jikinsa ya gaya masa ya san cewa abinda yayi ba dai dai bane ba kuma ya bata musu rai sosai saboda ya kiyayi gaba. Plan dinta shine sai yayi laushi sosai ya bada hakuri sannan ta saka shi a gaba yaje ya bawa Safina hakuri a gabanta sai kuma ta hada su su koma gida tunda alhamdulillah jikin su duk su biyun yayi sauki sai abinda ba'a rasa ba. In yaso ita sai da daukarwa safinan yan aiki tunda Mommyn ta tayi fushi ta kwashe nata. Kuma ita ta fahimci Mommyn sosai, dan idan ita ce in her shoes aka yi wa Mufida abinda akayi wa Safina ta tabbatar sai tayi abinda yafi wanda Mommyn tayi. Sai dai kuma ba ta jin zata kasance in her shoes din, dan halin Safiya da na Mufida ba daya ba ne ba. Sannan yanayin auren Mufida da na Safina ba iri daya bane ba. Amma kuma yau duk plans din na ta sun ruguje…..... She is no longer sure about what to do, Not after what Safina told her da yamman nan and also what Hajjo told her "Mama" Muhammad ya kira sunan ta a hankali bayan ta kai karshen surar da take karantawa. Ta dago kai ta kalle shi, gabanta ya fadi tayi sauri ta dauke kanta ta kalli gefe, kuka yayi, maybe tun dazu ne yayi ba yanzu ba but yau yayi kuka, Ba zata iya tuna ranar da taga dan nata yana kuka ba tun bayan girmansa. Wannan kam shine limit dinta, Already kullum zuciyar ta a karye take in ta ganshi cikin dakuwa ballantana kuma ace wai yana kuka? Muhammad Gidado? She can walk to the end of the earth to prevent that. She can walk to the end of the earth to put a smile on his face. "Mama" ya sake kiran sunan ta. "Mama dan Allah ki daina fushi da ni. Kiyi hakuri. In dai akan Safiyya ne na riga na gaya wa Abba cewa na hakura da ita. Tunda ba kwa so shikenan. I will accept duk abinda kuke so. Ni dai dan Allah ku daina wannan fushin" ta dawo da dubanta gare shi, ta sauke idonta akan abin karin ruwan da yake makale a hannun sa, yayi kokarin boye hannun, ta dauke kanta tace a hankali "kayi sallah?" Yace "eh nay)" yana mamakin yadda har yau bata daina yi masa irin wannan tambayar ba. Tace "kaje kaci abinci. Me zaka ci? Akwai tuwo kana so" ya dan bata rai, shi yadda yake jin makogwaronsa a rue baya jin ruwa ma zai wuce ta cikin sa ballantana tuwo, Ya girgiza kansa "na koshi" ta dauke idonta daga kansa sannan tace "ta shi ka je" ya mike ya fita yana hada hanya, amma a ransa yasan maganar bata kare anan ba. Ta bi bayansa da kallo har ya fita sannan ta sauke ajiyar zuciya. Kowa da irin kaddarar sa. This is not what they had planned for him, aure suka so suyi masa na gata, a lissafin su auren da wuri zai saka shi ya kara zama responsible mutum kuma ya kara masa himma gurin kafa roots din sa ya yi nasa family din and live happily ever after. Amma plans din su gabakidaya ya rushe sanda suka fahimci yarinyar da suka jima da sanin yana matukar so ta yaudare shi. A lokacin ne suka yanke shawarar samun wata su aura masa dan gyara barakar da suke ganin Safiyya tayi wa rayuwar sa, not knowing jefa su sukayi a cikin ramin da har yanzu ya kasa fito da kan shi. Amma yanzu ta dauri aniyar ganin ta saka igiya ta jawo kayanta da kanta, ko da kuwa duniya zata vi mata tofin ana tsine akan hakan. Sai da ta gama duk abinda zata yi sannan ta saka kayan baccin ta ta dora dogon hijab akai ta tafi kitchen, da kanta ta hada masa abinci marar nauyin da take ganin zai ya ci, noodles irin dahuwar da yake so, sannan ta hada masa hot chocolate yana tiriri. A’isha da ta tayata yanka vegetables din tana murmushi tace “Gaskiya zance da yaya karami (haidar) shima yayi rashin lafiya dan ake hada mashi wannan delicious din” murmushi kawai mama tayi bata ce komai ba sai kuma tace mata ta dauka ta kai mata kofar dakin Muhammad din. Ita kuma ta bita a baya. Sai da A’isha ta ajiye ta juya sannan Mama tayi knocking kofar, shiru ba’a yi magana ba, ta sake knocking shima shiru sai ta tura kofar ta shiga da sallama da tunanin ko yana toilet ne amma sai ta ganshi a zaune akan study table din sa da laptop a bude a gabansa. Hankalin sa gabaki daya yana kan screen din laptop din. Kasacewar ya juya mata baya ne ya saka itama ta tayashi kallon abinda yake kalla. Safiyya ce akan screen din, kamar video ne yayi mata tana zaune akan swing shi kuma yana tsaye a gefen ta yana dan tura ta da hannun sa kadan. Daga dukkan alama hira yake yi mata mai dadi dan sai murmushi take yi Amma Mama bata jin abinda yake cewa daga inda take tsaye. Yayi zooming fuskarta a lokacin da ta dan kwantar da kanta jikin igiyar swing din tare da lumshe idonta alamar hiran yana mata dadi. Sai a lokacin Mama ta kara tabbatar kyawun halittar Safiyya [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: Safiyya ce akan screen din, kamar video ne yayi mata tana zaune a kan swing shi kuma yana tsaye a gefenta yana dan tura ta da hannun sa kadan kadan. Daga dukkan alama hira yake yi mata mai dadi dan sai murmushi take yi amma Mama bata jin abinda yake cewa daga inda take tsaye. Yayi zooming fuskar ta a lokacin da ta dan kwantar da kanta a jikin igiyar swing din tare da lumshe idonta alamar lilon yana yi mata dadì. Sai a lokacin Mama ta kara tabbatar da kawun halittar Safiyya. Kyakkyawa ce ajin farko and she has a unique kind of eyes masu melting zuciyar duk wanda ya hada ido da ita, and her smile is contagious, da wahala tayi murmushi wanda yake tare da ita bai taya ta yi ba. Ya jima a haka yana kallon fuskarta Mama da take bayansa tana taya shi. Sai dai a cikin videon without warning sai Gidado ya tura swing din da karfi, ta dan yi karamar kara tare da bude ido cikin toro, ta kuma kankame igiyar a lokacin da lilon yayi sama da ita. Daga inda Mama take tana iya jiyo dariyar Gidado daga cikin laptop din, dariyar da ta jima bata ji yayi irin ta ba. Ta danyi gyaran murya, yayi sauri ya kife fuskar laptop din amma kuma bai juyo ba dan ya tabbatar ta gani. Sai data kira sunansa "Gidado" ya juyo da kujerar da yake kai amma bai daga ido ya kalle ta ba. Tace "kazo ka dauki abinci gashi nan a bakin kofa" ya taso ba tare da yace komai ba ya zo ya dauka ya koma kan kujerar ya zauna yana kallon abincin tare da jin soyayya mahaifiyarsa tana karuwa a ransa, "ka tabbatar ka cinye kuma ka sha maganin ka. Zan dawo in gani" yace "to" da murmushi a fuskarsa, yana mamaki kuma yana son yadda Mama take bashi umarni tare da treating dinsa kamar dan primary. Har ta juya sai kuma ta tsaya ta yi masa tambayar da dazu ta manta bata yi wa Hajjo ba "how did Safiyya's mother die?" Tambayar ta zo masa a bazata. Ya daga kai yana kallon ta amma kuma bai ga alamar wasa a fuskar ta ba. Sai a amsa, a ransa yana yiwa Safiyya godiya da ta gaya masa komai "she drawn" ya fada, sai kuma ya yi tunanin kara mata bayani "Safiyya ce ta fada cikin water reservoir when she was 2 years old, Her mother jumped in to save her. Ta fito da ita, ita kuma ta mutu a ciki",. Ta cigaba da kallon sa kamar ba ta fahimci abinda yace ba, amma ya fahimci maganar ta taba zuciyar ta sosai. Ta juya masa baya da sauri, maybe trying to hide her tears, sai kuma ta ce "goodnight" sannan ta fita. Part din mai gidan ta ta wuce direct, ta bude kofa ta shiga ta tarar da shi yana aiki akan computer, ya juyo yana kallon ta sai kuma yayi murmushi tare da daga hannun sa yace "na daina, na daina" ya san ta saka dokar cewa dare lokacin iyali ne da hutawa da kuma ibada, duk wani abu da za'a yi na neman duniya to ayi shi da rana. Amma sau da yawa ba bin dokar tata yake yi ba sai dai in ta kama shi ya bada hakuri. Bata kula shi ba dan abinda yake ranta ya fi wannan, sai ta wuce kan lounging chair din da take dakin ta zauna, yayi wheeling study chair din tasa zuwa gabanta ya tsaya yana kallon ta. Da karyayyiyar murya tace "dazu naji kace Gidado bashi da lafiya, me yake damun sa?" Abba ya dan yi mata murmushi "he will be okay kamar yadda na gaya miki, Rigima ce da taurin kai da ya dorawa kansa kwanan nan" ta gyada kai tana kara fuskantar inda maganar ta saka gaba "akan Safiyya ne ko?" Abba yace "yes. Kamar sun samu matsala ne I think. He told me wai sun rabu tunda bama so. Ita ma kuma wai babanta baya so. Amma na san fada kawai yake yi ba wai rabuwar suka yi ba" ta danyi murmushi, ita taga abinda ta gani yanzu a dakin sa. Ya danyi gyaran murya sannan with serious voice yace "kince zamu yi magana akan Muhammad. Wacce magana ce?" Ta danyi ajjiyar zuciya tare da cewa "kai ma ka fadi haka ai. You first" ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "yaron nan ba zai hakura da yarinyar can Safiyya ba. I think we need to look into other options than rabasu da karfi. A shawarce zan saka a yi min bincike akan yarinyar, sannan zan je inga mahaifinta inji shi menene take dinsa on all this tunda Gidado yace min shima ya hana yarinyar haduwa da shi. Ma'ana yasan abinda ake ciki kenan. Amma sai mun fara bincike akan yarinyar dan a lot of things don't add up about her", Mama ta dan girgiza kanta a hankali tace '"ba ka bukatar yin bincike, I have got all the informations we need about yarinyar" yayi shiru yana kallon ta da mamaki "how? When?" Ya tambaya dan ya san bata boye masa komai. Tace "dazu nayi magana da Safina, akan zancen komawarta gidan mijinta tunda jikin su duk yayi sauki. She told me wadansu maganganu da suka razana ni sosai" ta fada da karyayyiyar zuciya, ya bata rai, baya son bacin ran matar ta sa ko kadan, yace "wadanne maganganu kenan?" Ta girgiza kai "maganganun basu da muhimmanci. Surikar muce still. But she is not the right choiceor Gidado." Ta danyi shiru kamar yadda shima yayi yana kokarin fahimtar ta, sai kuma ta cigaba "sanda Hajjo tazo garin nan tazo yi mana murnar bikin su Muhammad ta ga pictures she told me ta san Safina, she told me they are family friends, and dazu maganar da Safina ta gaya min akan Safiyya ta daga min hankali har na fara mummunan tunani akan Gidado so l called Hajjo and asked her a favor, nace dan Allah ta gaya min duk abinda ta sani a kan Safiyya step sister din Safina. Farko kamar ba zata fada min ba, sai da ta fahimci hankali na a tashe yake kuma na gaya mata abinda yake tsakanin Gidado da Safiyya da kuma abinda Safina tace min akan safiyyan wanda har ya tayar min da hankali nake neman gaskiyar lamari, Sai ta saka nayi mata alkawarin ba zan gaya wa kowa a duniya ba, har kai, sai da nayi mata wannan alkawarin sannan ta gaya min komai". Ga mamakin sa sai yaga hawaye yana bin fuskarta, ta saka hannu ta share sannan tace masa "na riga nayi mata alkawari, bana son in karya alkawarin da nayi mata. Amma abinda zan gaya maka shine yarinyar nan Safiyya ta sha wahalar da ban taba gani ko jin labarin wadda ta sha irin ta ba. Ta fuskanci kaddara mai zafi. Kaddara kuma irin wadda zata iya fadawa a kan kowacce ya mace" ta danyi shiru still idonta yana kasa sannan ta sake cewa "ni mace ce, kuma ni uwa ce, watakila ku maza ba lallai ku fahimta ba amma ni na fahimta. Tunda har Allah ya sarke zaren kaddarar Gidado da na Safiyya har yanzu ta zamanto ita ce farin cikin sa, ni na amine kaje ka nema masa auren Safiyya ko dan mu samu ladan yarinyar nan sannan kuma mu samar da farin ciki ga dan mu". Ya dan girgiza kai cikin mamakin maganar ta yace "amma ba kya ganin this will be too much for him? I mean mata biyu at his young age? Kuma mata biyun ma makusantan juna? Zai fuskanci crises sosai a gidan sa" ta danyi murmushi "wannan kuma zabin sane, zama da su gabakidaya ko aka sin hakan zabin sa ne, mu namu shine mu sauke nauvin sa da Allah ya dora mana sannan muyi musu addu'a baki daya". Tana gama fadar haka ta mike ta cire hijab din jikinta ta rataye tare da hawa kan gado ta fara gabatar da addu'ar kwanciya bacci. Ya bita da kallo abubuwa da yawa suna yawo a cikin ransa. Duk da cewa shima tun dazu zuciyar sa ta fara karkata zuwa da wannan barin amma bai dauka tata zata chanja akala a lokaci daya ba. Me Safina tace mata? Me kawarta Hajjo tace mata? Baya son ya matsa mata har ta gaya masa tunda tace alkawari tayi cewa ba zata fada wa kowa ba har shi. Shi kuma zai so matarsa ta kasance mai cika alkawari. Sai dai in dai har zai aikata abinda ta ambata na aurawa Muhammad Safiyya, to dole ne sai ya san abinda taki gaya masa din, ko da kuwa ba'a wajenta ba ne ba. Da maganar ya kwana da ita kuma ya tashi, Da ita yaje office da ita kuma ya tashi, Wannan ya sa daga office din bai tafi gida ba sai ya gayawa driver dinsa ya kai shi gidan Alhaji Adam Muhammad, Ya san address din gidan ne sanda yana bincike game da Safina lokacin auren Muhammad. Mai gadi ya bude musu cikin sauri saboda gain kamalar sa, sai kuma ya tsaya yana kallon sa bayan ya fito fuskar sa tana nuna alamar ya gane shi, ko kuma ace ya gane waye shi. Ya kara gaishe shi cikin girmamawa sai ya gaya masa cewa gurin mai gidan yazo. Take ya ga fuskar sa ta dan saura cikin yanayin jimami sannan yace "baya jin dadi kam. Bashi da lafiya. Yau kuma kamar jikin ya matsanta masa dan tun safe babu wanda aka bari ya shiga gurinsa. Amma bara in fada a cikin gidan na san zasu san abinda za'a y" ya fada yana dosar Hussein da ya fito daga cikin gida da key din mota a hannun sa daga alama fita zai yi, suka dan yi magana da Hussain sai kuma Hussain din ya kalli Abba sannan ya koma cikin gida da sauri. Sai Abba yaji babu dadi a ransa, tunda bashi da lafiya bai kamata ya zo ya dame shi ba, Wannan ya sa ya sake kiran mai gadin ya gaya masa "zan koma kawai. Allah ya bashi lafiya, Zan dawo gobe ko jibi insha Allah" mai gadin ya gyada kai cikin fahimta sannan cikin girmama wa yace "zan gaya masa insha Allah, da zarar na samu ganin sa zan gaya masa" driver din Abba ya bude masa kofa ya shiga sannan suka fita daga gidan a nutse kamar yadda suka shigo. Hussain ya shiga cikin parlour da sauri, Mommy tana zaune tana waya da sister dinta da take aure a Kaduna "wallahi har yanzu bai ce min komai ba Sakina. Na rasa yadda zanyi. I tried all I can possibly do amma babu wata amsa. Yau ma gabakidaya ya kara rikicewa, ya ki ganin kowa ya hana kowa ganinsa sai Dr Ma'aruf. Shima kuma duba lafiyar sa kadai yayi amma bai ce masa komai ba". Tana cikin maganar Hussain ya shigo, ta lura magana yake son yayi mata sai tayi masa alama da hannu cewa ya fadi abinda yake son fada, yace "baban yaya Muhammad ne yazo, yana waje wai yana son ganin Daddy" cikin sauri tace "Sakina zan kira ki later" ta katse kiran tana kara kallon Hussain da shima yake tsaye yana jiran abinda zata ce "baban Muhammad kace? Wanne Muhammad din?" Ya dan bata rai "Muhammad din Safina mana, Shine yazo gashi can a waje yace yana son ganin Daddy, gashi kuma kinga Daddy tun safe yace kar wanda ya shiga gurinsa shine nazo inji me za'a gaya masa?" Ta mike da sauri kamar zata fita waie sai kuma ta dawo da baya "je ka sake duba Daddyn naku ka ga ko ya bude kofar" ya fita amma bata iya hakura ba sai ta bi bayansa tana jin dadi a ranta, at last iyayen Muhammad sun yunkuro da niyyar yin maganar da zata gyara auren yayan na su. Sam bata jin dadin yadda Safina take zama a gidan mijinta amma kuma ya zata yi? Dangin mahaifin su Safinan sun yi shakulatin bangaro da su kamar ma basu san da su a duniya ba, babu abinda zata ce sun tsinanawa yaran tunda mahaifin su ya mutu sai auren da suka daura wa Safina wanda a yanzu ba komai bane ba illa alakakai. Hussain ya dawo tun kafin ta karasa fita yana cewa "ya tafi. Ina jin Baba Ya'u ya gaya masa Daddy baya jin dadi. Har ya tafi" ta dan dafe kanta da hannun ta cikin nuna rashin jin dadin ta, ta so ace mazan sun zauna sun tattauna, wata kila zaman nasu ya samar wa da yarta ta mafita. Ta juya ta koma parlor ta zauna tana sauke ajjiyar zuciya hankalin ta gabakidaya yana kan halin da marayun yayan ta suke ciki. Kwana biyun nan ko bacci bata samu tayi saboda damuwa da take ciki da halin da yayan nata suke ciki, hanya kawai take nema da zata bi dan ta gyara musu rayuwar su ta samar musu da farinciki. Amma bata san wacce hanya bace ba. Ta zauna tare da sake sauke ajjiyar zuciya tana tuna maganar da Safiyya ta gaya mata few days ago, maganar tayi mata zafi amma kuma gaskiya ce, cewa auren ta da Adam kawai pretending suke yi but they are not happy with each other, because they lack the major ingredient of marriage, they lack love. Ta tuna da yadda auren nasu ya kasance, Hajiya ce ta hada su a ganinta zasu cike wa juna gurbin da suke da shi a rayuwar su. Farko duk sunyi rejecting saboda tunanin auren junan su kamar in amana ne ga marigayiya Safiya, amma kuma a hankali bayan an shekara biyu ana jeka ka dawo akan maganar sai suka amince. Safiyya ce sanadiyyar amincewar ta su duk su biyun, Ita ce a tsakiya. Tun sanda kasa ta rufe don Safiya bayan Adam babu wanda Safiyya take yarda dashi sai Sa'adatu, Tun Adam yana yakice Safiyya daga jikin Sa'adatu musamman sanda Hajiya ta fara yi masa maganar auren sa'adatun har daga baya shi da kansa yake kai ta gurin ta ta dan rike masa ita idan zaije wani meeting mai muhimmancin da ba zai iya tafiya da ita ba. Ta san cewa ya amince da auren ne ba wai dan yana son ta ba sai don yana son ya sama wa Safiyya uwa. Ita kuma a nata bangaren ta amince masa ne dan ta samarwa nata yayan uba. So it was just a transaction a tsakanin su. Kuma over the years duk kanninsu sunyi iyakacin kokarin su wajen ganin sun sauke nauyin yayan da yaje wuyan su. Duk d dai sun fuskanci challenges akan hakan dan Adam ya kasance mai matukar nuna soyayya ga Safiyya yadda baya hada ta da kowa baya hada ta da komai. Hakan ya jawo musu matsaloli da yawa, a hankali kuma ta fahimci cewa sam bai yarda da ita akan Safiyya ba, komai tayi mata idon sa yana kai, sannan baya taba neman shawarar ta idan zai yanke hukuncin duk da ya shafi Safiyya, kusan duk abinda ya shafe ta ma boye mata yake yi baya son ta sani, Hankalin ta bai gama tashi akan hakan ba sai da ya fara rashin lafiya, rashin lafiyar da aka tabbatar musu da cewa bata da magani. Few months after that sai gashi da theory din cewa kusan duk abinda ya mallaka mallakin Safiyya ne. Hakan ya sa tayi tunanin plan ne ya shirya dan ya mallaka wa Safiyya komai, ita kuma da yayan da ta haifa masa (twins) ko oho. Ballantana kuma agololin da tazo da su gidan. Tayi iyakacin kokarin ta dan gain an warware wannan kullin, har sai da ta tabbatar da cewa magana tabbas ce babu fashi sannan ta hakura. Amma kuma wannan sai ya sanya tsoro a ranta, tsoro mai girma, idan har haka ne idan mai kasancewa ta kasance da Adam to ya zata yi da yaya hudu? Biyu ma ta kasa rikewa a lokacin da take da kuruciva ballantana hudu a lokacin da girma ya riga ya zo mata? Wannan tunanin shi ya dasa toro a ranta shi kuma tsoron sai ya dasa wata idea a ranta, idea din hada auren Safiyya da Mustapha. Idan aka yi auren tabbas zasu samu security yadda ko babu ran Adam ba zasu tagayyara ba. Sai dai tun a bugun farko Safiyya ta debi kasa ta watsa a idanunsu tace bata so, Sai dai hakan bai sage mata guiwar ta ba, kamar yadda hakan bai hana ta zuwar wa Adam da maganar saurayin da Safiyya take son yazo gurinsa ya gaishe shi ba. Sai dai kuma taji dadin yadda yayi rejecting maganar tare da nuna cewa sai Safiyya tayi karatu mai zurfi sannan zata yi aure, a ganin ta wannan wani hope ne na cewa Safiyya zata iya yarda da auren Mustapha kafin lokacin. A haka kuma kaddara ta fada wa Safiyya, ciki ya bayyana a gare ya, wannan maganar ba karamin tayar mata da hankali tayi ba, tayi takaici kuma tayi bakin cikin kasancewar haka akan Safiyya, ta kuma tausaya mata halin da ta shiga lokacin da tayi niyyar zubar da cikin. Sai dai kuma a kasan ranta wannan ya kara mata hope, cikin Safiyya yana nufin more chances for Mustapha to marry her. Amma kuma cikin bai fita ba, sai ta boye maganar kin fitar cikin daga kowa da kowa, a ranta tana gayawa kanta cewa tayi hakan ne dan ta hana Safiyya cutar da kanta, dan kuma ta hana ta aikata zunubin zubar da ciki, amma deep inside of her tana ganin ta kara wa Mustapha chances of marrying Safiyya. With dan shege, dole na gida za'a aura mata dan a rufa mata asiri. And who is better to do that then Mustapha? Kuma cikin ikon Allah sai gashi Adam ya karbi maganar, amma Safiyya ta rufe idonta tace bata san zance ba. Har ma daga karshe ta zabi Mukhtar akan Mustapha din, shi kuma Adam as always, ya bi bayan yarsa. Ta sauke ajjiyar zuciya. Wannan abin ya kona mata ranta sosai, ta san cewa sun fahimci dukiyar su take so musamman yadda suke ta boye mata abubuwa, wai shekara da shekaru kayan Safiya da sarkokinta suna cikin gidan amma Adam bai taba gaya mata ba. Ita ma kuma tasan ba zata ce ta so Safiyya kamar yadda take son Safina ba, amma tabbas ta so Safiyya kuma har gobe tana son ta. Bata taba cutar da ita ba kuma bata jin ko nan gaba zata cutar da ita. Amma kuma tana son yayanta sosai, tana kuma son securing future din su da tata. Sai dai yanzu duk abubuwa sun rikice mata, har bata ma san ta inda zata kamo zarurrukan rayuwar yayan na ta ba ballantana ta tabbatar da ingancin sakar su. Safiyya taki auren Mustapha, ga Safina can kuma yana shan wahala a hannun mijinta saboda Safiyya, Safiyya….. Safiyyan kuma da a yanzu babu abinda zata iya yi mata dan tun daga ciyarwa har komai nasu ita da yayan ta ita ce take yi musu. Ta juya ta kalli hanyar dakin Daddy jin ana kiraye kirayen sallar magrib, tun jiya da ta yi masa sallama taje ta kwanta bata kuma saka shi a idonta ba dan tun asubar fari a rufe kofar sa ya ce babu wanda yake bukatar gani a ranar. Hatta Ahmad da yazo sai juyawa yayi ya koma ba tare da ya ganshi ba. Hatta yar lelen nasa Safiyya haka ta gama knocking kofa da kiran sunansa ta hakura ta koma sama ita ma ta rufe kanta. Ita dai bata san me ya same shi ba, tana kuma fatan ba wani laifin aka ce wani a cikin yayanta ko ita sunyi ba. Ya kori Mustapha yace babu shi babu shi har abada, saura kuma wa? Saura Safina? Ita ma yace babu shi babu ita? Ta mike tayi hanyar dakin tana addu'a a ranta, ga mamakin ta tana buga wa sau daya sai gashi ya bude mata shi da kansa, Ta shigo sai tuka wheelchair dinsa ya koma ciki ba tare da ya ce mata komai ba, Ta zauna tana kallon sa, kafin tayi magana yace "ina Hussain. Yazo ya taimaka min inyi alwala" ta dauko wayarta da sauri "bara in kira Hassan, Hussain ya fita" sai kuma ta ajiye wayar "ko inzo invi maka to ni?" Bai ce mata komai ba sai ta wyce ta dauko buta da bowl din da taga suna yi masa alwalar a ciki, tazo ta fara zuba masa ruwan tana kuma wanke masa gabobin alwalar sa harta gama yi sannan ta mike tana kallon sa. Tabbas akwai wani abu mai girma da yake damunsa, amma tana tsoron tambaya kar yace tazo ta bar masa gida irin yadda yace ranar da ya kori Mustapha. Ta saka towel tana rage masa damshin ruwan a jikinsa yadda ta ga yaran suna yi. "Dazu kayi bako. Mahaifin Muhammad yazo yana son ganin ka sai aka ce masa baka jin dadi" kallon da yayi mata sai ya saka ta tunanin in akwai abinda ta fada mai zafi, kamar ba zaiyi magana ba sai kuma yace "me yace? Da wacce maganar yazo?" Tace "bai ce komai ba. Amma ina tunanin maganar Safina ne. Kasan fa har yanzu tana gidan surukan bata koma gidan ta ba. Maybe zuwa yayi ya bada hakuri akan abinda yaron yayi sannan a nemi sulhu a tsakanin yaran", Ya juya kujerar sa ya kalli gabas sannan ya tayar da sallah ba tare da yace komai ba, Kafin ya idar ta fita, Ya juya yana kallon hanyar da tabi sannan ya daka hannu ya kuma daukan wayarsa da take gefen gadon sa, a hankali ya sake playing video din da ya kalla ya kai sau goma a cikin daren jiya da kuma wunin yau. Ya saka camerar din ne dan Safiyya, dan tana acting weird tana kuma boye masa abubuwa da yawa da yake son sani. Amma kuma bai taba tunanin allura zata tono masa garma ba. Yayi shiru yana kallon Safiyya da Muhammad a cikin screen din wayarsa, yana kallon su kuma yana sauraron maganganun su, yana kuma sauraron satin kukan safiyyan da yake ratsa ko'ina na jikin sa. Babu abinda yake so a duniya sama da ita. Babu kuma abinda ba zai bayar ba dan ya samar mata da farin ciki mai dorewa. Dan ya tabbatar cewa wannan kukan nata shine na karshe a rayuwar ta. Amma ya zaiyi....? Abinda take so din is close to impossible. Ya fahimci abubuwa da yawa a cikin video din, ciki kuwa har da cewar Safiyya ba zata taba samun mijin da zai so ta kamar Muhammad ba, shi bai ma taba tunanin akwai soyayya mai karfin irin wadda wadannan yaran suke yiwa junan su ba. Babu kuma abinda ba zai iya bayarwa a yanzu dan yaga sun auri junan nasu, ko da kuwa sauran numfashin da ya rage masa a duniya ne. Amma auren Muhammad ba zai yiwu ba sai da amincewar iyayen sa. Iyayensa kuma baya jin zasu aura masa Safiyya musamman idan suka ji kaddarar da ta fada mata. Shi kuma a matsayin sa na uban ta ba zai je ya roke su ba. In yayi hakan ya karasa zubar mata da guntun mutuncin ta a idon su. Zai jira ... Zai kuma yi addu'a. Addu'ar kuwa yayi yanzun ma, addu'ar Allah ya zaba wa safiyyan sa abinda yafi mata alkhairi a rayuwa. Yana shafawa Malam Ya'u ya shigo, ya gaishe shi sannan ya tabbatar masa da abinda Sa'adatu ta fada dazu "baban mijin Safina yazo dazu, na ga kamar maganace mai muhimmanci yazo da ita amma na gaya masa ba ka jin dadi sai yace a rabu da kai amma insha Allah gobe zai dawo ya ganka in ka ji dadin jikin ka" ya fada cikin girmamawa. Daddy ya sauke ajiyar zuciya tare da dawo da video din baya ya cigaba da sake kalla sannan a hankali yace "gobe? Allah ya sa muna da rabon ganin goben. In yazo goben zan ganshi insha Allah" Maman maman✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Fifty Nine : Chosen Her🧕🏻 Na saki labulen tare da komawa baya a hankali ina kuma rufe bakina da tafin hannuna. Tabbas Abban Muhammad ne. Amma me yazo yi gurin Daddy? Me yazo vi gidan mu? Me ya sani menene kuma bai sani ba? Na koma kan gado na na dauki waya ta and for uncomfortable time na kira number din Muhammad. Tana ringing, har tayi ta katse bai dauka ba. Tun safe haka nake fama. Nayi kiran nayi message din amma ya share ni. Jiya haka na kwana ban vi bacci ba kuma a jiyan wayar ta sa ma bata shiga sam, yau kuma tun sate tana shiga amma baya dauka. Na fahimci fushi yake yi da ni, na kuma san laifina kuma da mana san ransa zai baci in ya fahimci abinda nayi amma nayi wa kaina alkawarin kamar yadda nayi masa alkawari shima wanna insha Allah zai zama bacin ran mu na karshe, Bani da tabbas din plan dina zsi tafi smoothly amma abinda nake da tabbas akan sa shine addu'ar da nayi a kan lamarin, ina da tabbas din Allah zai amsa kuma zai warware mana komal cikin sauki kamar yadda ya zaba min Mukhtar sanda na roke shi kuma daga baya ya warware min aurena dashi cikin ruwan sauki, Na bude Whatsapp da sauri na tura masa message din da nake ganin zai dauki hankalin sa ya kula ni ko da kuwa bai huce da ni ba, in dai na samu ya kula ni ni nasan yadda zanyi ya huce din. "'Abba yazo gidan mu yanzu. I think gurin Daddy yazo". He saw the message kamar yadda ya ga guda goma sha dayan da na tura masa so far. Na ga ya fara typing kuma sai ya daina, sai kuma ya koma offline. Naji wani takaici ya kara mamaye zuciya ta hawaye ya kawo a ido na. Nan da nan na fara kukan kuwa. Ni da me zanji ne wai. Sai kawai na danna masa recording kukan nawa nayi tayi kamar karamar yarinya na tura masa, Ina kalion sanda message din ya je masa, ma ga kuma sanda yayi playing, he started typing again sai kuma ya daina. Naji kamar in jefar da wayar a kasa dan takaici. Sal na ajiye ta a kan gado na koma toilet na wanke fuskata sannan na zo zan wuce in fita daga dakin naga wayar tana blinking, da sauri na dawo da sure ta na bude hoping to see his name sai kuwa naga message daga gare shi. "Na samu sabon ring tune" Sai da na dan dora wayar a saman kirjina cikin nuna jin dadi na tare da lumshe ido sannan na bude na tura mass reply, "Ka wujjjiga zuciyata Muhammad. Gabaki daya na fita daga hayyacina a cikin wuni daya" "Let me see" "See what?" "The face. Data fita daga hayyacin na ta" Sai na gyara hijab din jikina tare da danna masa video call. Bai dauka ba sai yayi rejecting. "Can't answer..... Let me call you" Na rike wayar ina jujjuya ta a hannu na, wata zuciyar tana gaya min suna tare da Safina ne shi yasa yaki daukan kira na. Mintina kadan sai gashi ya kira ni video call Na jingina wayar tawa a jikin frame din gado sannan na kwanta ruf da ciki ian kallon wayar sai na answer. Yana dakin sa na gidan su a kan kujera, Kallo daya nayi masa na fahimci shima ya wujijiga kamar ni. Fatar idonsa tayi ja sannan sides din don sun tashi kadan. And his lips looked a bit dry. Direct nace masa "ba kayi bacci ba jiya ko" na lura studying dina yake yi shima sai yace "nayi. For like 3 hours I think. How are you?" Ban amsa ba nace "3 hours yayi kadan" ya daga kafada "ba laifi na bane ai. Me laifin ai ta san laifin ta" na kwabe fuska makar zan cigaba da kukan "na sani ai. Amma ai na baka hakuri. Dan Allah ni dai kar ka sake yin fushi da ni kaji? Gwara kayi min bulala Allah" na karasa ina jin hawaye yana kawo wa ido na. Yayi wanj gajeren murmushi da ban gane ma"anar sa ba kuma naji bana son sani, a hankali kuma yace "look at you. Kamar da gaske zaki daina din" nayi sauri cewa "Allah Yaya Muhammad da gaske nake, na daina bata maka rai kaji?" Na karashe cikin lallami, ya danyi shiru fuskarsa tana nuna har lokacin yana cikin bacin ral yace "but why do you do it?" Ya tambaya, sai nima na tambaye shi dan in tabbatar da cewa abinda nake tunanin ya bata masa rai din shine da gaske ya bata masa din "me yasa a karshen maganar mu ta jiya na gaya maka zan rabu da kai?" Ya girgiza kansa idonsa a kasa sai kuma ya dago tace "me yasa tun kafin mu zauna baki gaya min cewa zaki yi recording maganganun mu ba? We promised each other that zamu ke yin everything together a yanzu. You should have told me dan in san abinda ake ciki, I felt...........used". Ya karasa still da bacin rai a fuskarsa. Na gyada kai cikin fahimtar sa, amma sai nace "I promise I will explain everything to you. Amma yanzu dan Allah kayi hakuri kaji? Yanzu lokacin sallah yayi and zan sauka wajen Daddy idan nayi sallah. I will call you in na dawo daki and I will explain everything to you" ya gyada kai shina yana waigawa bayansa kamar wani ne ya shigo dakin, sai kuna ya juyo yace min "okay zamuyi magana in an jima" daga haka ya katse kiran Na ajiye wayar tare da kife goshi na akan ta na some seconds sai kuma na mike da sari yadida naji kiran sallah yana kara tashi a massilatai na shiga toilet. Bayan na 'idar na gabatar da adduoi na sai na sauka kasa kamar yadda na saba na tafi part din Daddy, babu kowa a parlour sai motsin Esther tana shirya dinner dining. Na wuce zuwa kofar shiga part din Daddy, tun safe ban ganshi ba, tun safe bai bari kowa ya ganshi ba dan haka bani da tabbas din cewa yanzun ma zan ganshi din. Kowa a gidan bai san dalilin hakan da Daddy yayi ba amma ni na sani, duk kowa yana cikin damuwa amma ni duk nafi kowa damuwa duk kuwa da cewa ina jin relief a wani bangare na zuciya ta cewa na gaya masa gaskiyar komai ba zai mutu da haushi na a ransa ba amma kuma bani da tabbas din hukuncin da zai dauka, Sai dai kowanne hukunci ya dauka na tabbatar ba zai yi hukuncin da zai zama cutarwa a gare ni ba. Na shiga parlour sa na tarar da Hussain a zaune daga alama daga masallaci va dawo, ya mike tsaye yana kallona cikin girmamawa sai nace "ya bude?" Ya dan gyada kai kadan "ya budewa Mommy da zu, amma ban sani ba ko ya kuma rufewa" nace "ba ka gwada shiga ba bayan ta fito?" Ya girgiza kai yana dan murmushi "Ke dai je ki gwada, toro nake ji kar ya sauke fada a kaina" na harare shi nayi hanyar corridor din da zai sada ka da bedroom dinsa. Na karasa bakin kofar na taba ta ina addu'ar Allah yasa ya bude, amma kuma ina tsoron facing dinsa after knowing what he heard and what he saw. Na danyi knocking kadan sai kuma na murda handle din na tura ta, naji ta bude sal nayi sallama tare da kasa kunnena, banji ya amsa ba, kuma dama yanzu ba'a fiya jin amsa sallamarsa ba tunda muryarsa tayi kasa sosai, dan haka kawai sai na shiga. Yana zaune akan kujerar sa, da wayarsa a hannun sa, naji gabana ya fadi amma sai na maze na nuna kamar damuwata gabaki daya akan halin da yake ciki ce. "Daddy" na karasa gurin sa da sauri. "Daddy ka hana mu ganin ka tun safe, duk mun damu" na durkusa a gabansa trying so hard not to look at screen din wayarsa. Ya saka hannu ya kashe hasken screen din sannan yayi ajjiyar zuciya tare da miko min hannu, na rike hannun nasa da hannayena duk biyun tare da dora guiwowina a kasa nace "Daddy are you okay? Wani abun yana damunka?" Sal ya danyi min gajeren murmushi, "I am fine Safiyya. Zuciyata tayi min dadi sosai. Ina fatan ke ma watarana zaki ji dadin taki zuciyar" na kara rikon hannun sa nace "a yanxu ma ina jin dadin zuciya ta Daddy. Knowing that you are happy kadai ya ishe ni farin cikj" a hankali yace "I have made a lot of mistakes Safiyya in raising you, Nayi kurakurai da dama. Addu'a ta kadai a yanzu ita ce Allah ya kara ara min lokacin da zan gyara su" na zauna sosai tare da zame hannu na daga cikin nasa, kai na a kasa nace "Daddy you did well, kayi iya kacin kokarin ka. Allah ya saka maka da alkhairi",. Muka danyi shiru kadan amma ina jin a jikina kallo na yake, sai kuma yace "kina da wani abu da kike so inyi miki? To put a smile on your gloomy face today? Tunda bani da tabbas din gobe" na danyi murmushi sai kuma na dago kai nace "Daddy ka dawo da Mustapha gida, he should be with you too, Bashi da wani gidan sai nan. Bashi da wani uban sai kai. Ban san laifin da yayi maka ba amma kayi hakuri". Ya sauke ajiyar zuciya yana kallon gefe amma bai ce min komai ba, a hankali na sake cewa "kaji Daddy na?" Ya dan kalle ni kadan ya sake dauke kai yace "ina twins? Suna ta nema na ko?" Na danyi murmushi "Hassan yana parlour, wai toro yake ji kar kayi masa fada idan ya shigo* ya danyi murmushi mai sauti yace Wit a min sh)" na tashi ina jin dadi a raina duk kuwa da naga Daddy bai amsa bukatar da na gabatar masa ba na leka nace "baban Daddy, Daddy yana magana" ya bude ido sal kuma ya mike da sauri yana magana a hankali yadda Daddy ba zal jI ba "shi yasa nace ki shiga, yana ganin ki zai sauko" nay dariya tare da talle masa keya, ya shiga yana sosa keyar na bishi a baya ina jin yana gayawa Daddy *Daddy ka ga ta dake ni ko?", Daddy ya mika masa hannu "zo nan babana" na karasa nima ina dariya. Daga baya sai ga Hussain ya shigo shima, sai kuma ga Mommy ta shigo ganin babu wanda yaje cin abinci, a karshe sai abincin aka hado aka kawo mana nan muka zauna muka ci a plate daya mu uku, Daddy yana kalion mu yana murmushi amma kana ganinsa in dai ka san shi kasan akwai abinda yake ransa. Mommy ma haka, tana tayamu hirar kadan kadan amma ita ma ranta duk a dagule yake kuma nasan Mustapha take missing. A lokacin ne kuma naji tana waya da Safina, Safinan tana gaya mata cewa a koma gidan mijinta, Ta ajiye wayar tare da jan tsaki tana kara bata fuska tace da Daddy "Safina ce. Wai an mayar da ita gida dazu, an kuma bata wata yar aikin. Ina in maganar komawar tata baban yaron yazo da zu kuy" Daddy ya juya ya kalle ta kadan sal kuma ya dauke kansa al ce komal ba ya cigaba da sauraron musun da ake tafkawa tsakanin Hassan da Hussain akan yan wasan ball. Duk hirar nan da akeyi Muhammad yana raina, na sam ya kira waya ta yaji ban dauka ba amma kuma bana son tashi saboda ina jin dadin zama da Daddy musamman idan naga yana wasa da twins. A haka har mukayi sallar isha muka cigaba da hirar mu, Mommy kam sai naga ta kwanta akan kujerar da take dakin ta rufe idon ta, naji babu dadi a raina, na san Safina da Mustapha ne a ranta and I felt bad for her amma sam ban ji regret akan abinda nayi ba. Sai da Dr Ma'aruf ya shigo sannan ya sallame mu yace mu bar Daddy ya huta, muka tashi muka fita muka bar su sai Mommy da ta zauna ita ma. Direct dakina na koma ina addu'ar Allah ya sa Muhammad bai sake yin wani fushin ba. Na je na dauki waya ta na kuwa ga missed calls din sa kusan two hours ago. Har na zauna na danna kiran sa sai kuma na tuna da maganar Mommy cewa Safina ta koma sai na kashe a raina ina gayawa kaina yana can yana angoncewa. Yes, na fahimci yaudarar sa tayi ta aure shi amma har yanzu ban manta da zancen cikin da tayi a gidan sa ba. Nayi kwafa na tashi na fara cire kayan jiki na. Sai gashi ya kira ashe wancan kiran nawa ya shiga. Na harari wayar ina gaya wa kaina cewa taimaka masa zanyi by not answering his call dan kar yashiga hakkin matar sa. Amma ni na san kishi ne. Sai da na shiga nayi wanka na fito sannan na sake ganin wani missed call din da kuma message. "Sarkin kishi" Na murguda baki kamar yana kallo na amma kuma ina jin kewar sa a raina ina so muyi magana dan akwai a lot of unsaid words a tsakanin mu. Sai da na gama dukkan shirin kwanciya bacci na sannan na hau gado nayi addu'a na rufe ido, so nake inyi bacci da wuri dan ina da abubuwan yi da yawa washegari wadanda suka shafi aiki na kuma ina bukatar clear head. Amma bacci yayi kaura daga idanuwa, kawai lissafe lissafe nake tayi, Nasan Daddy yaga video din can, wanne hukunci zai yanke akai? Me Abba yazo yi gidan nan? Da gaske maganar Safina ce ta kawo shi ko kuma wata maganar daban? Me Muhammad da Safina suke yi yanzu? Nayi tsaki tare da juyi, "Ya Rabbi" na fada a hankali kamar zanyi kuka, Sai kuma na jawo wayata na kunna data ina lura da yadda lokaci ya tura, Messages suka yi ta shigowa duk ban damu da su ba sal da naga nasa sannan na bude. *I called, ba kya kusa. Call me in kin gama" Ina gama karantawa na ganshi online. "Me kike yi baki yi bacci ba?" *Kar ka dame ni. Go back to your wife" "Hmmmm" *Fadi dai abinda yake ranka, kar maganar ta kumbura maka ciki" *Ban san me yasa kike nuna kishin ki akan ta ba, even after I told you yadda abin ya kasance" "She is still your wife, And you got her pregnant" “Hmmmm" “Kai ma hmmm” "Me kike nufi da hmmm din ta ki?" "Abinda kake nufi da taka hmmmm din shi nake nufi da tawa hmmm din" "To ai baki san me tawa hmmm din take nufi ba" "Me take nufi kuwa? In banda cewa maza rigar kaya ne ku?" "Lo!" '"Dariya ma kake yi ko?" "Okay to me kike so nayi? Can I call you please?" "Ni ba zanyi waya da mijin aure ba da daddare. Saurayi na zan kira wanda bashi da mata" "Hmmmm" "Kai ma hmmm" "Please in kira ki?" "This user is busy" “Please minti biyu kawai, So nake kawal inji muryar ki kince min goodnight baby" Kaje ta gaya maka baby din, ta goya ka da zani ma babu ruwa na” Na tura masa ina jin raina yana kara baci, ni yadda ya dauk maganar ba koma ba shi yafi komai bata min rai. Ina ganin sa yana typing na kashe data ta tare da jetar da wayar gefe na a kan gadon na ja bargo na lulube har kaina. A wannan daren shima da kyar bacci ya dauice ni. Washegari ina kan system tun safe ina all dan ko breakfast ban saulia kasa rayi ba sai dal Esther ta kano min, ina sane da Muhammad kuma na san ya kamata muyi magana in warware masa abubuna amma na cigaba da share shi. Har sal wajen azahar na kammala na tashi tsaye nayi mika duk jiina yana ciNio, wai dan mana samu tunda uncle Ahmad ya kora bakin aikin sa yana dan dauke min wasu nauye nauyen. Sai da na shiga toilet nayi wanka na shirya sannan na zauna na kunna wayata ina murmushi, ko babu komai na san jilin sa -ya gaya masa zuNa yanzu, ba dai shi mai mata ba? Himmm Ina kunnawa sai ma hau yan danne danne na, a haka na shiga Instagram na fara scrolling through feeds, a lokacin ne naga wani post a wani blog da naga yaja hankali na saboda tarin comments din da akavi akan sa. Sai na samu kaina da karantawa. Irin yan hide my ID din nan ne, na karanta labarin tun daga farko har karshe sannan na sake karantawa sai kawai na samu kaina da dariya. Mamakin Safina yana kara kamani. Tun a karantawar farko na gane ita ce. Wai tana neman shawara ne agun malamar blog din da yan comment section, wai step sister din ta tana neman raba ta da mijinta. A labarin nata yadda ta nuna shine a gurin dinner dinta ne muka hadu da Muhammad, wai tun daga nan na makale masa shi kuma ya juya mata baya, babu irin wulakancin da baya yi mata akaina. Tace a wayarta ma ya dauki number ta kuma ya gaya mata baki da baki cewa number ta ya dauka. Sannan bayan ta samu ciki yace baya so saboda yana ganin in suka haihu za'a hana shi aure na, yace sai ta zubar taki shine ya mare ta ya kuma ture ta da mota ta fadi cikin ya zube kuma taji ciwuka. Maganganu dal iri iri, Ko comment section din ban shiga ba na wuce na cigaba da abinda yake gaba na. Mani da lokacin ta ballantana na bloggers Sal na fita ma na koma na Kira mijin nata sai bayan da ya dauka sannan a tuna ashe fushi nake yi dashi, duk kuwa da cewa ban san abinda yayi wanda yasa nake yin fushin ba. Da ya dauka kuma si nayi shiru. Shima daga bangaren sa sai yay shiru din muk cigaba da sauraron numfashin juna. A raina nace zanga wanda zai fara sauko wa tsakanin ni da kai, Shi din ne kuwa ya fara magana "wai ni ya akayi wanna lamarin ya juye ne? The last time I checked ni akayi wa laifi nake yin fushi ana bani hakuri har da yi min kuka. Yanzu kuma lokaci daya na samu kaina a mai bada hakuri bayan ban san laifin da nayi ba kuma ban gama hucewa daga laifin da aka yi min ba" na murguda baki *oho. Nima ban sani ba" na kuma yin shiru, yayi ajjiyar zuciya "to shikenan. Kiyi hakuri. Whatever it is. I am sorry, shikenan?* Nace "shikenan. Kai ma kayi hakuri. Na san nayi ba dai dai ba amma ina saka ran dan nayi maka bayani zaka gane insha Allah* ya danyi shiru sannan yace *why do jou do it? Why were you recording our conversation kuma meyasa baki gaya min zaki yi hakan ba before you do it” Na danyi ajiyar zuciya nace "I wasn't recording.... Yace "then someone was listening. Maganganun ki na karshe sun nuna min cewa ba dani kike magana ba, da wani kike magana. Waye?" Nace "Daddy" duk muka yi shiru, sai ya maimaita "Daddy? How?" Sai na bashi labarin cctvn da Daddy ya saka a ko'ina a gidan sa da niyyar kamani tunda ya lura kamar bani da gaskiya ina boye wani abu, and how I used that to my advantage wajen warwarewa Daddy duk abinda nake ganin ya karata ya sani a game da alakar mu. Yayi shiru har na kai karshen bayanin nawa sannan yace "and why didn't you tell me before? Yadda zamu zauna mu shirya komai tare?" Na ce "I wanted to do that. Amma kuma idan na gaya maka your reactions won't be real, I wanted to show Daddy the truth and the depth of your love for me, and I did. Kayi hakuri Baby. I believe wanna maganganun da Daddy yaji tsakanin mu su zasu kawo mana karshen issue din mu with him. Insha Allah ina ran zai fahimta" Na danyi ajiyar zuciya nace "I wasn't recording.... Yace "then someone was listening. Maganganun ki na karshe sun nuna min cewa ba dani kike magana ba, da wani kike magana. Waye?" Nace "Daddy" duk muka yi shiru, sai ya maimaita "Daddy? How?" Sai na bashi labarin cctvn da Daddy ya saka a ko'ina a gidan sa da niyyar kamani tunda ya lura kamar bani da gaskiya ina boye wani abu, and how I used that to my advantage wajen warwarewa Daddy duk abinda nake ganin ya karata ya sani a game da alakar mu. Yayi shiru har na kai karshen bayanin nawa sannan yace "and why didn't you tell me before? Yadda zamu zauna mu shirya komai tare?" Na ce "I wanted to do that. Amma kuma idan na gaya maka your reactions won't be real, I wanted to show Daddy the truth and the depth of your love for me, and I did. Kayi hakuri Baby. I believe wanna maganganun da Daddy yaji tsakanin mu su zasu kawo mana karshen issue din mu with him. Insha Allah ina ran zai fahimta" Ya danyi shiru kadan kamar yana tunani akan maganar sannan yace "na fahimce ki, na kuma karbi uzurin ki, but please Piya let this be the last time da zaki boye min magana. Please" a hankali nace "insha Allah. Kayi hakuri. Wannan shine bacin ranka akan wanna maganar na karshe. Kaji?" "Hmmm" kawai yace, nace "ka hakura?" Yayi ajiyar zuciya "ya zanyi? Ya zanyi da ke Piya? Ba na iya fushi da ke duk yadda naso inyi hakan kuwa. Yanzu wannan fushin da nayi me ya faru da ni? Ba gashi nan kuma ni nazo ina bada hakuri ba?" Nace "ai issue din da ka bada hakuri a kansa daban ne ba wannan bane ba. Wannan ai ni na bada hakuri akan sa tunda nice nayi wannan laifin" yace "okay ni akan wanne na bada hakurin kenan?" Na dan bata rai nace "ka sani ai. You are just refusing to admit it" yace "because I don't believe abinda nayi laifi ne, but still na bayar da hakurin ai ko? And one day insha Allah, I will explain it to you" nace *One day? What day?" A hankali yace "idan lokacin yayi you will know" nace "hmmm" ya danyi dariya "what?" Nace "kai fa yanzu ka gama yi kin preaching akan being open to each other da sauran su. And now you are closing up" ace '"akwai abubuwan da are sensitive...." Nace "sensitive? Abin da zaka fada min ya kal wanda na gaya maka zama sensitive?" Sal ya sake cewa "hmmm" sannan sal yay kokarin chanja topic yanzu dai kina so kice min duk maganar da muka yi shekaran jiya Daddy yaji? Na fahimci chanja layi yayi Amma ita ma maganar da ya dawo kanta mai muhimmanci ce Nace “ba ji kadai nayi ba, har gani yayi” muka sake yin shiru sai naji yace “oh my god” dasauri, nace “what?” Ya sake cewa “ya salam” kamar hankalin sa a dan tashe, Nima nawa hankalin ya fara tashi nace “what? Mene ne ya faru?” Yace “kin ce ya ga komai” nace “yes, ya gani, am sure. Menene ya tada hankalin ka? Yace “at a point there. There was a point that we……that we were……”na gane abinda yake magana akai sai na ajiye wayar nima cikin tashin hankali, naji kamar kasa ta tsage in shiga “na shiga uku” na fada a fili, na kuma daukan wayar da niyyar mu tattauna mu nemi mafita sai naji yana dariya, nace “dariya fa kake yi? Ka shigo gidan Daddy har falon sa kayi hugging? Ka san halin Daddy kuwa? Ya dai na dariyar yace “point of correction. His daughter hugged me” da sauri nace “I didn’t. I didn’t” yayi dariya sosai “ko mu karbo video dan daga hannun daddy mu duba?” Nace “a karbo mana, kowa ya gani ai zai gane. It wasn’t…… I wasn’t…..I was trying to stop you” ya cigaba da dariya hankalinsa a kwance, nace "at least nawa is justified. Na ka kuma fa?* cikin dariya yace "it is justified too. I was trying to console you, rarrashin ki nake y'* ya fada da confidence, nace "okay haka zaka ce masa ko? To babu ruwana ni dai" muka yi shiru, sai kuma yace "kin san Allah ne ya kama mu? We have never done something like that, ranar da mukayi kuma a matsayin kuskure a ranar ne aka kama mu. Maybe dan Allah yana son mu ne, it is a warning to not do it again". Muna ta yin hira sai ji nayi ana kiran sallar la'asar, dole muka rabu dan amsa kiran ubangijinmu ba wai dan mun gaji da junanmu ba, na ajiye wayar ina muirmushi, one thing about soyayyar mu da Muhammad ita ce duk tashin hankalin da muke ciki to as long as we are together sai muji kamar bamu da damuwa ko kadan, Sai da nayi sallar laasar sannan na sauka kasa, a lokacin naga mommy tana zaune a dining tana ta juya cokali a hannunta, na zauna na gaisheta ina kalionta yayin da Esther take hidimar zuba min abinci, Sai da ta gama ta tafi sannan nayi mata magana "mommy nayi wa daddy maganar Mustapha, insha allah zai huce nan bada dadewa ba, Yanzu ma in na sake korawa gurinsa zan sake yi masa magana. Kuma • ta watsa min wani kalion da yasa na mayar da sauran magana ta cikin cikina na kasa fito da ita. *kamar yadda kika yi masa magana ya kore shi?" ta fada a hankali maganar kamar ba daga bakinta ta fito ba, na rufe ido na na bude ina jin babu dadi a zuciyata, idan nace ban son mommy nayi karya, sam bana jin dadin yadda alakar mu take komawa, Na dago kaina a hankali nace mata "wallahi mommy bani na ce ya kore shi ba. Ta yaya zan ce masa ya kore shi? Shima nan ai gidan su ne, insha allah.....* "cut it" ta dakatar da ni, "bana son jin komai daga gareki, daga baban naki nake jiran jin bayanin da zai yi sannan in san wanda nima zanvi" sai ta tashi ta bar abincin ta ta fita, nima ji nayi duk abincin ya fita daga kaina. Na jima ina kokarin ganin naci, amma ganin hakan ba zai samu ba sai hakura na tashi zan koma sama dan bana son cigaba da zama a kasa ballantana mu sake yin sa'in sa da mommy. Sai dai ina shiga parlor Hussain ya shigo da saurin sa *mommy, baban Muhammad ya dawo, gashi can a waje yace a gayawa daddy yazo" mommy ta mike daga kwanciyar da tayi da sauri tare da daukan mayafin ta da Yake ajiye a gefe, Hussain yace "ba sai kin tashi ba mommy, ki bari zan shigar da shi, gaya miki dama kawai zany* ta girgiza kanta " uhm uhm, barni inje inyi masa bayani sosai, kasan baban naku ya zama a lallaba yanzu” na bita da kallo har ta shiga part din Daddy sai na wuce Hussain da sauri na koma sama naje na daga labule ina kallon Abba, yana tsaye a jikin motarsa looking as majestic and elegant as ever, wani irin kwarjini yana fita daga jikin sa, a gefen sa Haidar ne a tsaye yana ta kalle kallen gidan. Gabana faduwa kawai yake yi da sauri da sauri, shin da gaske maganar Safina yazo yi? Ko wata maganar ta daban? Ko Daddy zai yi masa maganganun mu da Muhammad? Sai na koma cikin dakina na da sauri a lokacin da naga Hussain yazo yayi musu iso suka doshi kofar shiga part din Daddy daga waje. Nayi dialing number din Muhammad ina binsu da kallo har suka shiga sannan ya dauki kiran, tun kafin yayi magana ne “Abba ya dawo yanzu ya shiga gurin Daddy” he sound surprised, “ yanzu?” Nace “yes, yanzu suka shiga. Kasan me ya kawo shi?” Ya danyi shiru, “he mentioned something shekaran jiya akan zaizo gurin Daddy. But ban dauka soon zai zo din ba. Let’s wait and see me zasu ce.” Nace “tsoro nakeji” yace “tsoron me?” Nace “kar Daddy ya nuna masa wannan videon” yace “what about it? In yayi haka ya rage mana aiki shima ko?” Nace “baka gane ba….. there is that part a ciki” ya danyi dariya “that part where you were hugging his son?" naji hankali na ya kara tashi "dole ma in sace wayar daddy". Ina nan ina gadin hanya ina jiran fitowar Abba amma shiru, sai daga baya na lura bada Haidar suka shiga ba, dan naga alamar shima ya gaji da jira ya dawo waje ya zauna akan kujera, daga baya ya mike ya koma cikin mota, Duk abinda ake yi ina updating Muhammad wanda yake makale a kunne na. Shima daga gurin aiki ya tashi yana hanyar sa ta komawa gida. Sai da aka fara kiran sallar magrib sannan Abba ya fito, Haidar ya fito daga cikin motar da sauri ya bude masa kofa ya shiga shi kuma ya tuka suka fita daga gidan. Na sauke ajjiyar zuciya sannan na gaya wa Muhammad, daga nan nay masa sallama na tafi da shirin yin sallah nima, Ina idarwa na sauka kasa na zauna a parlor ina ta baza kunne inji ko wani zaiyi min maganar baban Muhammad da yazo. Ashe bani kadal bace ba, mommy ma baza kunnen take yi dan itama Daddy bai barta ta zauna tare da su ba, amma daga Hassan har Hussein babu wanda ya san komal akan zuwan nasa. Daga baya dai da ta fahimci ba su ji komai ba sai ta tashi ta shiga gurin Daddy da kanta. Ta jima a ciki sannan ta fito fuskarta tana nuna damuwa, ta dan zauna kadan sai kuma ta tashi ta hau sama tana waya da mustapha. Nima ina son shiga gurin Daddy kamar yadda nake vi duk dare amma kuma sai na kasa, zucivata cike da fargaba, A karshe dai na tashi na shiga saboda nima ina son ganin sa, ba zan iya kwanciya bacci idan ban ganshi ba. Na shiga dakin nasa da sallama kamar kullum, yana kwance nurse dinsa yana goge masa jikinsa domin vi masa shirin bacci, ya miko min hannu kamar kullum yana murmushi, na karaso na saka hannu na a cikin nasa sai yace "naga baki shigo ba, da yanzu zan aika a kira ki. Ina so ki shigo muyi magana kafin inyi bacci" nayi kneeling a gabansa nace "gani daddy, akwai abinda kake bukata ne?" ya girgiza kansa kadan "alhamdulillahi, babu abinda nake bukata a yanzu. Allah yayi min komai Alhamdulillah" na gyada kai ina murmushi nima nace "Alhamdulillah" sai yace "sai dal akwai abinda nake so in gaya miki" na hadiye wani abu a kirjina nace "menene daddy?" yace " kamar yadda kika gaya min cewa kin hakura da wancan yaron, kuma kin bani damar in zaba miki mijin da zaki aura ko wanene, na fitar miki da miji safiyya, and you are getting married as soon as possible insha allah" Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Sixty: The Reward Assalamu alaikum, Ina barar addu'a a gurin ku, na rasa cousin dina shekaran jiya da daddare. Allah ya ji kanta ya kai rahama kabarin ta tare da sauran al'ummar musulmi baki daya. Ameen Na ji wani abu ya tokare min a makogwarona, sam ban yi tsammanin wannan maganar daga gare shi ba a yanzu, na cigaba da kallon sa ba tare da na bude baki ba ballantana inyi masa magana, shima kallon nawa yake yi, sai kuma naga a hankali ya saki hannuna sannan ya saka hannu ya goge min fuska ta, sai a lokacin na fahimci hawaye ne yake fita daga ido na, nayi sauri na goge da nawa hannun sai yace "kiyi addu'a" na gyada kai da sauri sai kuma na tashi nayi masa sallama na juya da na koma cikin gida, Addu'ar da yace inyi ita nayi tayi kuwa. Zuciyata tayi min wani irin nauyi. Miji? Aure? Na san yayi min maganar aure kuma na san babban burinsa a yanzu da kullum yake ganin kamar ba zai kara kwana daya a duniya ba shine ya ga nayi aure, amma ban dauka da kanshi din zai zabar min ba kamar yadda ni da kaina na ce masa na amince, musamman ganin cewa sanda za'a yi min wancan auren ma na fari kuma ga laifin da yake tunanin nayi a lokacin amma duk da haka sai da ya bani zabi. Na dauka wannan karon ma zabin zai bani amma zai hada da Muhammad a ciki tunda ya fahimci gaskiya yanzu. Nayi ajiyar zuciya, babu abinda nake son ji a yanzu sai abinda Daddy da Abba suka tattauna a zaman da suka yi na fiye da awannin biyu. Me suka ce? Me sukayi? Wanne hukunci suka yanke? Na dauki waya ta ina kalion lokaci, thinking if it is right to call Muhammad a wanna lokacin. Tunanin haka kuma sai yasa kishi ya kara tokare min zuciyata. Ina tsananin kishin Muhammad dan addu'a ce kawai take kwantar min da zuciya ta a duk lokacin da na tuno cewa yana auren Safina har yanzu, Kuma suna da dukkanin rights din da ma'aurata suke da su for each other. Nayi tsaki tare da ajiye wayar na fara shirin kwanciya duk kuwa da cewa akwai wadansu aiyuka da zanyi kafin in kwanta din. Ina cikin shirin naji waya ta tayi kara amma ba Muhammad bane ba, na dauka na duba naga sunan Mustapha. Har nayi niyyar ba zan dauka ba sai kuma nayi tunanin why not? Na dauka da sallama. "Hankalin ki ya kwanta ko?" Ya fada ba tare da ya amsa sallamar ta wa ba. Nayi ajjiyar zuciya sannan na zauna a bakin gado nace "dama na san you will accuse me of this" yace "to idan ba ke ba waye? As far as I know ban taba yi wa Daddy wani babban laifin da zai ji zafi na har haka ba. Ko kira na baya amsawa. Wai waye baya kuskure ne? Me yasa zaki yafewa Mukhtar ma amma ni ki kasa yafe min?" Nace "ba lallai ka yarda ba. And believe me, right now yadda abubuwa suka cunkushe min, I don't even care ko ka yarda ko kar ka yarda. Amma ni na yate maka ba tun yanzu ba, abinda nace kawai shine ba zan aure ka ba saboda ba zan iya zaman aure da kai ba. Maganar Daddy kuma ni da bakina ban je gurinsa na gaya masa abinda kayi min ba, ballantana har ince ya kore ka. Kuma bayan ya kore ka ma naje na roke shi ya dawo da kai, kuma ban hakura ba zan cigaba, amma ba dan kai ko dan halin ka ba sal domin shi da Mommy" Na katse kiran tare da jan tsaki ina jin raina yana kara baci. Mutane suna da saurin judging other people but not themselves. Kowa yafi jin dadin rufe laifin sa ya kalli na wani. Sanda muna magana da Mustapha naji shigowar kira, na kuma san muhammad ne amma da muka gama wayar ban duba bama dan bana son va fahimci ina cikin bacin rai, bana son ya san abinda yake tsakani na da Mustapha dan ina fatan nan gaba komai zai wuce kuma ina fatan zasu samu fahimtar juna watarana. Sai bayan da na gama dukkan shirye shirye na sannan na dauki wayar amma ban kira shi ba sai na hau online, ina zuwa na tarar da message dinsa already a can. "Me Daddy yace?" Nayi murmushi, he is as much concerned as lam, "Nima ban sani ba, Bai gaya min komai ba a kan haduwar su da Abba. Abba bai ce maka komai ba?" Naga message din yaje masa amma bai bude ba,. Na ajiye wayar ina tunanin ko in Kira shine? Sai kuma na fasa, Maybe yayi bacci, maybe kuma yana tare da matarsa, Nayi tsaki tare da jan bargo na rufe har kaina. Mintuna kadan kuma sai na bude na sake daukan wayar na nemo number din sa na kira, tayi ta ringing sai kuma naji an dauka amma kuma ba'a yi magana ba. A take na fahimci cewa ba shi bane ba, zuciya ta ta gaya min cewa in katse kiran amma kafin in katse sai naji tace "waye? Yana wanka ne, matarsa ce take magana" Sai na katse kiran na ajiye ina jin kamar ana gasa masara a kirjina. Jiki na ya bani ta san nice and she said that to hurt me kuma tayi nasara. I though she will call back amma sai naji shiru. Sai da aka jima sannan na sake jin ya kira ni, na share shi da na gaji da jin karar wayar ma sai na saka ta a silent nature ta gefe ina hawaye. Da assuba ma ina idar da sallah naji kiran sa, nayi tsaki, a raina nace "ka koma gurin matarka kaji duminta kafin rana ta fito. Munafiki" na sake yin tsaki "namiji! Namiji!" Na nade kayan sallahta na koma gado na kwanta, naji shigowar message, sai kuma na jawo wayar na duba message din a raina ina tunanin ai ba zai san na gani ba tunda sms ne, "Please ki dauki waya. Akwai wani albishir da zan yi miki mai dadi" Sai kuma ya sake kira, kamar ba zan dauka ba kuma sai curiosity yayi getting the better of me, na dauka amma ban ce komai ba sai yace "albishirin kj' nayi shiru amma zuciya ta tana bugawa, ko Abba ya gaya masa wani abu ne? Yace "baki ce goro ba" a hankali nace "ka fadi abinda zaka fada ka koma gurin matarka" ya danyi dariya, wani takaici ya sake kama ni, wato ya kira nine kawai dan ya yi min dariya, nan take na fara hawaye "au dama kira na kayi kayi min dariya ko? Kai ba ka damu bama da abinda nake ji a raina, you don't care". Ya dan gyara muryarsa da take dauke da alamun bacci yace "one day you will be here on my bed and I will tell you the story of what happened yesterday night and you will laugh too, kinji? Believe me abin dariya ne ba na damuwa ba. Kinji sweetling?" Na goge hawaye na da hannu na nace "to ka gaya min yanzu mana in da gaske kake yi. Me yasa sai ranar da baka da tabbas din zuwanta?" Yace "ina ji a jiki na cewa zata zo mana Piya, Ina ji a jiki na nan ba da dadewa ba zaki zama mallaki na" sal ga murmushi yana replacing hawaye na. "Abba yace maka wani abu ne?” Yace “bai ce min komai ba, nayi ta binshi amma ko maganar baiyi ba min ba sai Haidar naji yana gayawa Mama ita ma sai ta share maganar. Daddy bai ce miki komai ba?” Na danyi shiru sannan nace “bai ce komai ba akan zuwan Abba. Amma ya gaya min wata maganar daban” yace “wacce maganar? Me yace?” Nace “yace Wai ya zaba min miji, kuma zai daura min aure nan ba da dadewa ba” muka yi shiru gabaki day sai yace “are you thinking what I am thinking?” Na danyi murmushi “yes. yes I am” ya danyi karar murna “yes!” Nayi dariya sosai “zaka tayar da makota daga bacci fa” yace “let them them wake up. Kowa ma ya tashi bacci yakare” Nace “ba lallai ne abinda muke tunani shine ba fa” yace “think positive” na sauke ajiyar zuciya amma still ina jin hankali na bai kwanta ba, sai dai murnanar da yake yi ta sanya ya min rai sosai, yace “su fa sun dauka suna playing din mu ne, basu san mu muka je fa kwallon a field din ba” nayi murmushi “idan suka gane kuwa zasu iya fasa abinda suka fara” yace “ai manyan mutane ne, basa magana biyu, indai har sunce yes din shikenan magana ya kare”. Mundade muna hira, har sai da gari yayi haske sosai sannan yayi min sallama tunda zai fita gurin aiki, sai a lokacin na tambaye shi "wal wanne albishir ne kace zaka yi min?" Yace "to ai baki ce goro ba, shi yasa na fasa gaya mik'" nace "goro" yace "I love you, Shine albishir din, I love you so much" na lumshe ido na na bude ina jin kamar bani da wata damuwa duk duniya, sai kuma nace "and i love you too by Baby" sai kuma na katse kiran da sauri na kife wayar tare da rufe idona ina zabga murmushi kamar tababbiya, sai kuma na fara jejjefa kafafuwa irin yadda yara suke yi in suna murna daga nan kuma sai na mike tsaye akan gadon na fara tsalle, sai da nayi mai isa ta sannan na fadi na kwanta akan gadon ina mayar da numfashi na. Wata zuciyar ta tambaye ni what if ba shi bane zabin Daddyn? What if Abba da Daddy basu daidaita ba and Daddy yaji haushi yayi deciding on someone else? Nayi sauri na kawar da tunanin tare da maimaita abinda Muhammad ya gyaa min dazu "think positive". Na tashi na saka hijab dina akan dogayen kayan baccin jikina na fita, yau saboda farin cikin da nake ji ni zan yiwa yan gidan nan gabakidaya breakfast. A kitchen na samu Esther har ta fara peeling potatoes, na dauko kajl daga freezer na fara akin su ni kuma, muna yi muna hira da dariya and she mentioned that yau ma that person ne ya kuma saka ni farin ciki, ranar ban boye mata ba kawai sai na gyada mata kai amma ban kara komal akan hakan ba Bayan mun gana mun jera komai a dining sai na koma sama zan shirya ita kuma ta fara hidimar gyaran gida, sanda na kuma saukowa duk mutanen gidan sun tashi, muka wuce dakin Daddy na fara gaishe shi tare da kissing cheeks dinsa sannan na bi su twins duk nayi kissing dinsu na koma kan Mommy ita ma nayi mata kuma na rungume ta, ta janye ni tana kallon fuska ta da alamar tambaya amma sai na share. A lokacin ma sai da na kara yi wa Daddy maganar Mustapha, twins suka taya ni rokon sa and he said he will consider it. "Zai dawo, amma ba yanxu ba. Akwai abinda nake jira", Mommy tana kallon mu bata ce komai ba. Ranar haka na wuni da murmushi a fuska ta Muhammad a makale da ni a waya yana ta yi min nacin yana son gani na amma na gaya masa babu dama, tunda na gaya wa Daddy cewa na rabu da shi bana son yin wani abu ko yaya ne da zai nuna wa Daddyn cewa karya nake yi. Kuma a wani bangaren na zuciya ta har yanzu ina tunanin kallon don Muhammad after maganganun da muka yi ranar nan. Da yamma sai ga Uncle Ahmad, ya shigo ciki muka gaisa sannan ya shiga gurin Daddy suka jima suna magana sannan ya fito shima da murmushi a fuskar sa, "God is really amazing" ya fada a lokacin da yake yi mana sallama. Muka bishi da ido ni da Mommy har ya fita sannan Mommy ta tabe baki "ba dai za'a taba chanjawa tuwo suna ba, komai gyaran da za'a yi masa kuwa". Ranar na zo kwanciya bacci sai ga message from one of my guards "Mukhtar was seen lurking around this area. Be careful". Na alive wavar tare da yin ajiyar zuciya. Mukhtar bashi da hankali tabbas, yana kuma son ya kure nawa hankalin. Sun riga sun san abinda zasu yi in suka kama shi, dan haka ban sake maimaita musu ba. Haka kwanaki suka yi ta wucewa, babu wanda aka cewa komai a cikin mu daga ni har Muhammad, shi na fahimci hankalin sa a kwace yake amma ni sam nawa ba'a kwace yake ba except idan muna waya da Muhammad. Gani nake ba Muhammad ne Daddy ya zabar min ba, gani nake yi Muhammad is too good to be true with me dan ni na saba da bad news, bad news na sani tun kafin haihuwa ta dashi na saba dan haka good news din sounds weird to me. Kwanaki biyar bayan zuwan Abba sai ga Uncle Sufyan yazo gidan mu, nayi murnar ganin sa sosai na gaishe shi sai kuma nayi ta kalion bayan sa ko zan ga Aunty Hajjo ta shigo, sau yace min "ba tare muka z0 ba aj" sai naji kunya ina fatan ba wai yana nufin Junior nake nema ba, ni kuma har ga Allah Aunty Hajjo nake nema, maimakon ita sai Abdul naga ya shigo da leda a hannun sa, na gaishe shi shima sai gaishe da Mommy tare da miko min ledar hannunsa sa "tsaraba" yace yana murmushi, na karba nayi masa godiya sai suka wuce gurin Daddy. Na bude ledar, kayan ciye ciye ne kawai iri iri, exotic biscuits and chocolates. Na mika wa Mommy "gashi Abdul ya kawo min" ta tabe baki "ni kika ga ya bawa?" Sal naji babu dadi, na cigaba da tsaiwa da ledar a hannu na sai tace "abinda vasa aka kala wa Mustapha wani sharrin kenan aka kore shi, Abdul ake so a dawo da shi. Kuma na san wanna duk hadin Ahmad ne, Dan dan sa dan akuya ne ya san ba za'a mayar masa da ke ba shine ya kwaso Abdul. Ai shikenan". Na juya ban ce mata komai ba na koma sama, bana son obsession din Mommy akan hada aure tsakani na da Mustapha, wannan obsession din shi ya rufe mata ido gabakidaya. Ya kamata ace ta gane bana so ne kawai kuma hakan baya nufin bana son ta ko yayan ta, baya nufin kuma zan daina kula da su. Auren Mustapha ne bana so and there is no amount of nagging da zata yi da zai saka in chanja. Amma kuma bayan na koma daki na bude one of the biscuits ina ci sai wani tunani ya fado min, what if Abinda Mommy ta fada akwai gaskiya a ciki? What if Abdul Daddy ya zaba not Muhammad? Na fito da biscuits din bakina da sauri na zubar a waste bin sannan naje toilet na wanke bakina ina kallon kaina ta mirror, "Ya Rabbi" na fada a hankali. Tun daga nan kuma sai hankali na ya tashi, A gidan suka karasa wunin ranar, har sai da suka ci abincin dare sannan suka tafi. Banji dadin yadda na hadewa Abdul rai ba duk kokarin da yayi na ganin munyi hira sanda na sauka gurin Daddy, na ga kuma shima bai ji dadin hakan ba a fuskarsa amma kuma I couldn't help it. Ya zanyi idan maganar Mommy ta kasance. Ranar sai da nayi kuka kafin inyi bacci amma ban yarda na nuna wa Gidado ba duk kuwa da yaso ya fahimci ina cikin damuwa, Washegari Friday sai ga Uncle Ahmad da sassafe muna breakfast ya shigo da kansa yana tambaya ko akwai abinda ake bukata na cefane a gidan, yace za'a yi baki ne in an jima bayan sallar juma'a. Mommy ta tambaya su nawa ne vace bai sani ba kawai dai ayi abinci da yawa kuma na fita kunya. Bata ce masa komai ba amma da aka jima sai gasu sun dawo shi da yaya da ledoji cie da kaji da vegetables ta fruits. Sai kuma kwalayen lemuka na alfarma. Mommy ta tashi ta shiga gurin Daddy sai kuma ta fito ranta a bace ta hau sama. Hakan ya sa na fahimci ba zata yi girkin ba, dan haka na cire hijab dina muka shiga kitchen nibda Esther muka kama aiki, muna cikin aikin Hussain ya shigo shima na tisa keyarsa zuwa kitchen din na bashi aiki, Hassan ya shigo shima na jawo shi, tun suna bata rai har suka saki jiki muka yi ta aikin muna hira Hassan har da kunna kida yana rawa. Sai da muka ci karfin aikin sannan muka sallame su dan kar su makara masallaci mu kuma muka karasa Abinci kam munyi shi, friend rice da taji Kayan hadi da kuma hanta, sai mandi rice Ita kuma de aka hada ta da gasashshen naman ragon da yayi laushi sosai, sai kuma muka yi brown superghetti da kuma cheese macaroni, sai tuson shinkafa miyar zogale sannan sakwara da miyar agushi, Sa peppered chicken da salad, Sannan fruits. Mun yi aiki kam mun gaji sosa), dan ma kowanne variety ba wai da yawa muka yi sosai ba amma munsan zai isa tunda abubuwan da yawa, Muka gama juye komal a warmers, muka ware na abincin gida muka Esther ta kai dining ta jera ni kuma na fara kokarin hawa sama sai gata ta dewo tana cewa wai ai bamu gama ba tunda bamu yi farfesu ba, *Abinci baya zama complete sai an hada da pepper soup" na harare ta, ssi kiyi tayi, ni dai ba inji bace ba kuma na gaji, ke kika ce ba kya so a kawo miki mai taya ki aik™️" La dega kafada "indai farfesu ne yanzu kuwe zanyi, akan sa za'a hada ni da wata? Ai kuwa gwara in kwana ina yin farfesu, kala biyu zanyi ma ko uku. Haka kawai?” ta koma kitchen tana mita ni kuma na girgiza kai kawai na koma daki. Dana shiga sai na tsiri aikin gyara kayana ina kokarin Cire zuciya ta daga tunanin bakin Daddy, su Waye? Me kuma ya bata ran Mommy haka? Sam bana jin dadin bacin ranta. Sai na fita na tafi dakin ta na tarar da ita a falon ta na sama a zaune tana waya, “wallahi sakina na gaji da halin mutumin nan. Allah hakurin da nakeyi ba kowacce mace zata iya irin sa ba. Sam Sam baya ganin daraja ta da kima ta, dani da babu duk daya. Kawai daga tambayar su Waye bakin da zasu zo sai ya fara neman gayamin magana……” sai na juya na koma ba tare de na karasa shige ba, Ina komawa dakin sai kawal na cigaba da gyaran kayan da na fara, amma still zuciya ta tayi min nauyl, ban gama ba kuma sai na barshi na shiga toilet nayi wanka na fito ina tunanin kiran Muhammad ko naji muryarsa inji dadi amma kuma sal na tahimel lokacin masallaci ne, dan haka sai na barshi na shiga closet dina na dauki abaya mai dogon wando na saka ba tare da na yi wata kwalliya ba except for mai da turare, lokacin na san an gama fitowa daga masallaci, Amma still ban kira Muhammad ba sai na tayar da sallah, sai dai banjima da tayar wa ba naji alamun motoci suna shigowa gidan mu, nayi kokarin yin sallah ta a nutse sannan nayi addu'a na shafa sai kuma na mike na daga labulen tsegumi na na leka waje. Bakin motoci na gani guda uku, Ban san ko daya daga ciki ba. Sai motar uncle Ahmad da ta uncle Sufyan. Na ci gaba da kalion motocin ina jin faduwar gaba a karshe ma kawai sai na koma na zauna a bakin gado ina kallon hoton Ammie rungume da ni. A hankali nace "Hey Ammie". Wayata naji tayi kara alamar shigowar sako, na dauka da sauri ina tunanin ko Muhammad ne amma sai naga alert ne daga banki na, personal account dina, bana expecting wani kudi da zai shiga ciki dan haka na bude, na tsaya ina kallon kudin, sannan na kalli sunan wanda ya turo min kudin "Abbakar Sadiq Abdallah" ban taba jin sunan ba tun da nake, sai kuma na kalli caption din "sadaki". Gaba na yayi wata irin faduwar da sai da na zamo daga kan gadon na zauna a kasa, Abbakar Sadiq Abdallah? Waye wanna kuma ni Safiyya? Na shiga uku. Kar dal ace Daddy aure na ya daura da wanna mutumin da ban ma taba jin sunan sa ba. Karar waya ta ce ta dawo da ni hankali na, na dan zabura kadan saboda tsoratani da karar tayi, tun kafin in dauka na san Muhammad ne, wayyo Muhammad, innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Amma kuma sai nayi tunanin bara in dauki kiran nasa inji yana ina, watakila zan samu wani bayani daga gare shi. Na dauka na saka a kunne na ban ce komai ba sai naji muryarsa fes a kunne na, kamar ma a hanya yake "hey sweetling. Kin ganni yau a kafa na tafi masjid saboda in samu lada" na dan dake nace "kana ina yanzu?" Yace "ina hanyar komawa gida, are you okay? You sound not okay" sai kawai na katse kiran tare da ajiye wayar a gefe na. Ina jin shi yana cigaba da kira na amma ban dauka ba. Waye wannan Abbakar Sadiq din? Menene dalilin Daddy na hada ni da shi? Da gaske an daura min aure da shi? Na cigaba da zama a gurin kamar gunki har adadin mintuna ko awannin da ban sani ba, Sal kuma naji anyi knocking kotar dakina, automatically nace "shigo" ba tare da nayi tunanin waye ba, kamshin turaren da naji ya saka na juva, Uncle Ahmad ne, ya ci kwalliyar sa cikin manyan kayan da daga gani sabon dinki yayi ga hular sa ya saka da tayi matching da kayan sa, fuskarsa kamar gonar auduga, kallo daya nayi masa na dauke kai, kowa ma haushi yake bani. Ya shigo sosai ya zauna akan kujerar da take dakin tana kallon gadona shima yana kallona yace "Safiyya" na daga kai na kalle shi na mayar da kaina kasa, yace "kinga sako kenan?" Na gyada masa kai kawai, sai ya sake yin murmushi yace "yaya ya gaya min cewa kin bashi wuka da nama, kince kin amine ya zaba miki koma wanene yake gain shi ya dace da ke. Ya kuma zaba din, nima kuma na aminta da zabin na sa bayan yayi min bayanan dalilin yin zaben. Na shigo ne yanzu in gaya miki an daura miki aure yanzun nan" yayi shiru muna jin alamar fitar motoci daga harabar gidan. Yace "Allah ya sanya alkhairi ya yi miki albarka" sai ya mike tsaye, nayi sauri nace "uncle waye...….???" Sai kuma na kasa karasa tambayar, ya karasa min "waye angon? Kar ki damu, zai zo in an jima da daddare sal ku ga juna, Ina so ki saka a ranki cewa duk duniya babu wanda yake son ki sama da Adam kuma ba zai taba zaba miki abinda zai cutar da ke ba" ya kai bakin kofa na sake tambayar sa "uncle an gaya wa Mommy?" Ya daga kafada "mijin ta ne ya yanke wannan hukuncin, shine kuma zai gaya mata da bakin sa. Ni ba za'a ji mutuwar sarki a baki na ba". Na bishi da kallo ina kokarin digesting maganar sa. Kiran da ya shigo wayata ya katse min tunanin na dauko wayar ina kallon sunan Muhammad ”pyar💕” sai kawai na katse kiran tare da kashe wayar gabakidaya na ajiye ta sannan na tashi na gabatar da sallar la'asar din da ake tayi a masallaci, ni dai ba zan iya cewa ga abinda nake ji zuciya ta ba dan wani irin zafi da zugi take yi min. Da na idar da sallar ma sai na kasa yin addu'a mai tsaho kamar yadda na kasa yin kuka, kawai na zame na kwanta a kan sallayar na lukluba da hijab din jikina ina jin sanyi yana ratsa kasusuwa na. Anan na cigaba da kwanciya har aka yi sallar magrib, babu wanda ya leko gurina nima kuma babu wanda na nema, naji ina missing Ammie sosa da sosai, wai aure aka daura min yau. -Na tashi duk da sanyin da nake ji na je nay alwala na dawo nayi sallar magrib sannan na cigaba da zama akan sallayar ina ta kiran sunayen ubangiji da niyyar ya kawo min dauki ko ya kawo min sassauci a zuciya ta. Ina nan zaune naji an sake turo kofar an shigo tare da sallama, na juya da sauri jin muryar da nayi kamar daga sama, Muryar Aunty Hajjo, na bita da kallo har ta karaso cikin dakin ta kunna fitila tana kallona da murmushi a fuskar ta "amarya" na sunkuyar da kaina ina fatan hawaye zasu zo ido na ko zan samu sanyi a zuciya ta, na kasa ko da gaishe ta ne, ta zo gaba na tare da kamo hannuna ta rike a cikin nata tace "k gaishe ni ba zaki yi ba? Ke fa kika ce kin ba da zab'" ta fada cikin tsokana, na bude bakina da niyyar gaishe ta amma muryar taki fitowa sai na mayar da kaina kasa, tace "ki tashi ki shirya ga angwayen can sun zo zapsu ganki" na sake dago ido da sauri na kalle ta sake yi min murmushi sai nayi sauri na girgiza kaina "ni ba zan je ba. Ni bana son zuwa. Ni ban san shi ba. Ni bana son shi" sai na ga ita dariya ma abin ya bata. "Ya akayi kika san ba kya son sa bayan ko ganin sa baki yi ba?" Ni dai ban ce mata komai ba amma na san ko waye shi ba zan so shi ba dan babu wani space a zuciya ta da Muhammad bai cika ba. Ta matsa wai lallai sal na tashi na shirya na chanja kaya, na tubure mata taga ina neman inyi mata dan karamin hauka sai ta rabu da ni tun da ta lura kayan jikina ba wai sunyi muni bane ba, amma sai ta kwaso turare tayi ta fesa min har sai da naji yayi min yawa a kaina, sai kuma ta nemi mayafi mai dan girma ta lullube ni da shi ta kama hannu na muka fita. Muna fita daga dakina na juya ina kallon hanyar shiga part din Mommy, a hankali nace da aunty Hajjo "Mommy fa?" Ta kalli kofar tace "tana gurin Daddyn ki" daga haka ta ja hannuna muka sauka kasa. Ni dai ina kankame da hannunta jikina sai rawa yake yi kaina a kasa har muka sauka, naji alamar akwai mutane kuma maza a falon saboda maganganun da suke yi kasa kasa amma muna gama saukowa suka yi shiru, ban daga kai na kalle su ba sai ma sake shigewa jikin Aunty Hajjo na yi wadda ita naga kamar ma abin dariya yake bata, da kyar ta jawo ni daga bayanta ta tsayar dani a gabanta sannan a hankali kamar mai rada tace min "ta yaya zaki ga angon naki idan baki daga idon ki ba?", A hankali na daga idon na nawa, zasu kai su shida ko bakwai a falon duk da ban tsaya kirga su ba. Na fara kallon su daya bayan daya, duk da murmushi akan fuskokin su, a fuska ta biyu naga Haidar, yana kallona da murmushi a fuskar sa, najl zuciya ta ta buga da karfi, a take na bude luska ta sosal a fara baza idon neman sa, and then I saw him, smiling brightly from ear to ear, hasken hakoransa yayi matching da hasken fararen kayan jikinsa wadanda suke kyalli da sheki kamar yadda fatar jikinsa take yi. Sai na ga kamar gabakidayan sa ya zama tamkar farin wata dan daren goma sha biyar. Ya mike tsaye idanunsa suna kyalli, reflecting the love he has for me, sannan a hankali ya bude min hannayensa. Na saki hannun aunty Hajjo, ba tare da na jira komai ba, ba kuma tare da na damu da tarin mutanen da suke gurin ba, na wuce straight zuwa kirjinsa sannan ya mayar da hannayen ya rufe ni a ciki. A take na saki kukan da nake ta fatan zuwan sa tun lokacin da aka daura auren. Ina jin yadda gabakidaya falon ya rude da hayaniyar da take nuna murna. Maganganu suke yi hade da dariya gabakidayan su a lokaci daya amma bana jin abinda suke fada, bana jin komai sai sound guda biyu a lokaci daya, daya na bugun zuciyar shi da nake jin ta kamar a cikin kunnena take bugawa, dayan kuma na murmushi mai sauti da yake fitarwa wanda nake jin sa tamkar a cikin kwakwalwa ta yake yinsa, sai naji wannan mix na sautuka tamkar shi ya fi kowanne sauti dadin sauraro. Ya kara matse ni a jikinsa da hannu daya, sannan ya saka daya hannun a hankali yana bubbuga baya na dashi alamar rarrashi, sannan a cikin kunne na yace "it is okay. Ya isa haka. Muhammad Gidado is here. You are okay kinji?" Na daga kai a hankali na kalli fuskar sa kamar mai tabbatar wa da cewa shi din ne ba wani ne ba, ya sunkuyo da kansa shima muka kalli jina cikin ido sai kuma nayi saurin mayar da tawa fuskar kasa ina jin kamar numfashi na zai dauke, we have never been this close, I have never been this close to any man. Aunty Hajjo ce tayi gyaran murya, sai naji kunya ta kama ni kamar zan nutse a kasa, da sauri na kara jawo mayafin jikina na kara rufe fuska ta dashi, tace "wanne rufe fuska kuma zaki yi? Ni da kika manta da ni ma? Babu komai ai yau na san matsayi na" mutanen gurin suka yi dariya, nima nayi tare da kara sunne fuskata a kirjin Muhammad, tace "babu komai mu hakan da ma muke fata, Sako ne dama na zo isar muku da shi inji parents din ku. You are a reward to each other for being good kids. Fatan su kawai tare da mu gabaki daya shine ku cigaba da zama yaran kirki. Allah kuma yayi muku albarka". Gabakidaya aka ce Ameen, ta juya zata tafi, na bita da kallo sai idona ya sauka akan Daddy a can kofar shiga part dinsa, yana zaune akan wheelchair din sa idonsa a kaina fuskar sa dauke da murmushi. A hankali nace masa "thank you" ta hanyar motsa bakina yadda babu wanda yaji sound din sai shi da yake kallo na. Ya gyada kai sannan ya daga hannun sa yayi min thumbs up sai kuma ya juya ya koma cikin part dinsa ya rufe kofa. Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Sixty One: Selfishness Not Edited Him👳🏻‍♀️ One week ago Idan yace a cikin nutsuwa yayi wannan sati to tabbas yayi karya, daga shi har duk wanda yake tare da shi ya tabbatar cewa ba'a nutse yake ba. Sau da yawa mutanen da suke tare da shi sukan tambaye shi "are you okay?" Sai dai ya gyada musu kai kawai ya sharar da maganar dan baya son yin karya kuma baya son yin bayanin abubuwan da suke damun sa din. Na farko akwai labaran da Safiyya ta bashi na gaskiyar abinda ya faru da ita, gaskiyar abinda ya jawo ta rabu da shi a wancan karon. Zai iya cewa tunda ya zo duniya bai ta ba jin abinda ya daga masa hankali ba irin wannan maganar, wannan tashin hankalin ya janyo har likita ya gwada jinin sa kuma ya tabbatar masa da cewa yana gab da samun cutar hawan jini, Sai na biyu kuma fahimtar da yayi cewa duk maganganun da suka yi da Safiyya Daddyn ta ya gansu kuma ya ji su, wannan ma ya saka shi cikin damuwa dan bai san wanne mataki Daddyn zai dauka akan abinda yaji kuma ya gani ba. Will he be satisfied cewa ya cancanta ya bashi yar sa kamar yadda ya fahimci Safiyya tana saka rai ko kuma zai raba su ne for the second time. Ian kuma hakan ta kasance anya kuwa zuciyar sa zata iya dauka? Anya? Sai dai kamar yadda Safiyya tayi shima sai yabi hint dinta, sai ya sanar wa da iyayensa duk biyun cewa ya hakura da auren Safiyya tunda basa so, amma kuma ba wai dan shi baya so ba, ya kuma nuna musu irin damuwar da wanna hukunci zai jawo masa, sannan kuma sai ya cigaba da addu'a ba dare ba rana akan fatan Allah yay guiding iyayen na sa su zaba masa abinda yake mai alkhairi a gare shi. Abu na uku kuma da ya dame shi a cikin satin shine yadda Mama ta rufe idonta tace ya tattara matarsa su koma gidan su ta gama jinyar su. Haka yana ji yana gani ya dauke ta a mota da kayan ta ya kai gida. Dadin da yaji a wannan bangaren daya shine yadda Safinan ta dauke mass wuta gabadaya ko kallon inda yake bata yi ba tunda ta shiga motar har ta sauka, shi kam sai yaji hakan yayi masa dadi sosai. Suna sauka kuwa kowa ya kama gabansa. Abu daya ne yake kwantar masa da hankali a duk wadannan al'amuran, shine waya da Safiyya. In suna waya manta wa ma yake yi da kowa da komai ballantana har ya tuna da wasu problems da suke tattare da kowa da komai din. Duk da son da yake yi ya ganta amma haka ya hakura saboda babu dama. Duk kuwa da damuwar da yake ciki haka ya daure ya ke nuna mata bashi da damuwa dan baya son taji damuwar sa tai breaking down. Shine namiji dan haka shi zai zama strength din ta Sanda ta bashi labarin zuwan abban sa gurin Daddyn ta yayi mamaki dan Abban bai ce masa komai akan hakan ba. Ranar ma bayan sun gama waya haka ya tafi gida yayi ta zama ko zai ji abban ya ce masa wani abu amma sai yaji shiru babu bayani. Ranar kuma da ta gaya masa abinda Daddy yace mata akan ya zabar mata mijin aure sai ya nuna mata yana murna, ya nuna mata yana tunanin shine wanda Daddy din ya zaba, yayi hakan ne dan va qa alamar zuciyar ta cike take da doubts amma kuma a zahirin gaskiya ta sa zuciyar ta fi tata raunana akan lamarin Sai ya ga kuma hakan ya yi lifting spirit dinta sosai ta kuma dan saki jikinta suna cigaba da faranta wa junan su rai but kowa a cikin su akwai doubt din shi. His second major concern aside not having Piya is what to do with Safina. Safina have been like a thorn in his heart tunda ya san ta ya san wacece ita, bai taba tunanin zai iya wulakanta mutum kamar yadda ya wulakanta Safina ba, bai kuma taba tsammanin akwai macen da zata dauki abinda Safina ta dauka daga gare shi ba. She did everything she did saboda tana sonsa, or rather because she is obsessed with him, dan shi bai yarda abinda take ji a kansa soyayya ce ba. At the end kuma, she lost everything. Wannan shi yasa yake jin tausayin ta a kasan ransa, musamman bayan tayi miscarriage, duk da cewa ba da ne ta haita ta kuma rasa ba amma ya san a matsayin ta na uwa already ta so abinda ya zauna a cikin ta, Wannan ya sa yake daga mata kafa yanxu sosai, ya daina yi mata kallon wulakanci ¡ya kuma daina gasa mata bakar magana, ya kan shiga gurin ta kullum ya dauki kudi ya bata ya kuma tambaye ta in akwai abinda take so. Sai kuma ya fahimci ta fara daukan hakan a matsayin wani abu daban, har ta dawo da yi masa girki wanda tun a ranar farko da ta yi masa ya gaya mata ta daina "ba ci zanyi ba, barnar abinci kuma babu kyau" hakan ya sosa mata rai sosai har ta zubar da kwalla ta sa ya kuma jin tausayin ta but he stood his ground, any na farko anyi na karshe, yanxu kaffa kaffa yaje yi da sha ko cin duk wani abu da yake gidan dan gudun kar a kuma, kar ta kara samun damar yiwa rayuwar sa illa. Sai dai kuma Safina wata halitta ce wadda a duk lokacin da kaji tausayin ta sai tayi wani abun da zai saka kaji tausayin kanka for jin tausayin ta. Ya fahimci rawar kafar da take tayi a kansa tunda ta fahimci ta fara samun sassauci a gurinsa, kwalliyar ta dawo, saka matsatstsun kayan sun dawo, amma shi yasan ba zai iya bata abinda take so ba, ba zai iya ba, wannan shi ya sake tuna masa cewa dole ya san yadda zaiyi ya rabu da ita as soon as possible dan idan ba haka ba zata jashi zuwa wuta for not fulfilling her sexual desires as her husband, A bangare daya kuma har yanzu bai cire Mukhtar a ransa ba, Safiyya tace yayi mata alkawarin ba zai taba shi ba amma ko a lokacin bai yi alkawarin ba, kuma baya jin zai iya. Wani irin rage yake ji a ransa a duk lokacin da ya tuna da shi. Ya san kuma rage din da yake ji just need a little push zai yi exploding, push din kuma might be as little as seeing Mukhtar din. anar Monday yaje gidan su kamar yadda ya saba yi duk sanda ya tashi daga aiki, sai dai tun a waje ya ga motar Uncle Faruk a harabar gidan su, bai ma san uncle din nasa ya zo gari ba dan haka ya shiga cikin gidan da murnar sa dan yayi missing din shi. Amma sai dai yana shiga ya ga Mommy (his grandma) a zaune a falo tare da Abba da Mama da kuma shi uncle Faruk din. Ya kara fadada murmushin sa, ba zai iya tuna ranar da yaga Mommy a gidan su ba, bata zuwa sai dai su je gurinta, "Matar" ya fada da murmushi "yau auren ne ya kawo ki har gidan nan? Ko biko kika 20 dan kinga kwana biyu ban leka kin ganni ba?" Ta watsa mass harara "ohh Wali nan kai namiji ne? Namijin da har za'a y) biko idan yayi yaji?" Uncle Faruk yana dariya yace "maganar gaskiya dai Mommy bikon kika z0, kinga kyakkyawan saurayi kim kasa zama sai da kika biyo shi har gidan su" ta tabe baki "ina abin yake? Zama kyawawa ai sun kare. Tun da mijina ya mutu babu wani namiji da zai burge ni anan duniya". Gidado ya karasa gaban su yana jinjina soyayyar Mommy da marigayi Muhammad Dikko. Babu yadda za'a yi ayi magana da ita bata saka shi a ciki ba. Ya durkusa ya gaishe ta amsa tana kare masa kallo daga kasa har sama, sai kuma ya juya ya gaishe da Uncle Faruk amma sai uncle din ya mike ya jawo shi jikin sa ya rungume, Gidado ya lunshe ido yana jin zuciyar ss tana yi masa dadi, yana son yan'uwan sa sosai. Har ya koma ya zauna Mommy tana bin sa da kallo, sai da ya zauna sannan ya kalle ta tare da daga mata kafada "what?" Bata amsa masa ba sai ta juya gurin Abba "gashi nan ai abinda na gaya muku tun ranar nan kuka mayar da magana ta wasa, jibi yadda matar can ta zuke yaron nan, kunga yadda ya koma kuwa? Haka gidadon yake? Yaro ya kare gabakidaya ya lalace maimakon ace yayi kiba yayi annurin aure amma shi sai bushewa da naga yayi * Mama tace "Mommy kin manta bashi da lafiya ne? Accident fa yayi, har yanzu dinkin da aka yi masa a kansa bai gama warke wa ba, daga baya kuma ya kwanta rashin lafiya again" Mommy tace "dama haka zaku ce ai. To waye ya saka yayi accident din? Ai Maimoon ta gaya min komai abinda ya faru, kuma waye ya saka ya fara rashin lafiyar? Ba damuwa aka ce tayi masa yawa ba? Me zai saka shi damuwa in da yana samun kwanciyar hankali da iyalin sa? Gaskiya da sake. Ai na ga ba kwa daukan abin da muhimmanci shi yasa nace auta ya kawo ni har gidan naku dan ku fahimci muhimmancin magana ta" Abba yace "Mommy rashin lafiya ai daga Allah ne ko? Ai wani baya saka wa wani rashin lafiya" ta harare shi tace "Allahu Akbar. Mai karatu na gaba" ta nuna Mama "ke zaki dora daga inda ya tsaya? Aya zaki jawo min ko hadisi?" Mama ta girgiza kai da sauri sai uncle Faruk ya yi dariya, Mommy ta juya ta watsa masa harara sai ya dauke kansa gefe yana kunshe sauran dariyar sa. Mommy ta cigaba "magana daya ce nazo da ita, Yaron nan aure za'a sake yi masa. Ga jikoki nan kyawawa Allah ya hore min su, in ma baya so a cikin su yaje ya zabi wacce yake so a waje ya kawo in dal tayl a aura masa ita. Ba zan zauna ina kallo a cutar min da jika ba wallahi. Haka kawai ba zai kare yarintar sa cikin wahala dan ya faranta muku ba". Abba ya yi gyaran murya ya fara magana cikin lallami dan ya fahimci sosai mahaifiyar ta sa ta dauki zafi. "Mommy ki kwantar da hankalin ki. Mun riga mun gama magana da ma da Zainab akan issue din yaron nan. Har ma na yi waya da Habib da Moon nace mu hadu yau a gidan ki mu tattauna akan maganar dan mu tsayar da shawara daya. Amma tunda kinzo nan din kuma kinzo da maganar ba ra in kira su kawai sai ince su taho nan gidan, tunda ga Faruk ma yana gari... Tace "auren za'a yi masa dai k0?? In ba wannan maganar bace ba bana son jj" Mama tace "auren za'a yi masa Mommy. Insha Allahu in muka yi miki bayani zaki fahimta" Mommy tayi ajiyar zuciya "zan saurara inji. Duk wani hukunci da za'a yanke ina nan zaune zaku yanke shi. Ba zan barku ku sake daukan wani shirgegen aikin ku hada shi da shi ba. To me yayi zali shi ba wuta ba? Haka kawai santalelen saurayi kamar wannan a tashi a dabaibaye rayuwar sa a guri daya a hana shi zaben abinda yake so. Ni ba dan Ayaan ya riga yayi maganar Khausar ba da Gidado zan bawa" Faruk yace "wai ya batun Bassam kuwa? An gano inda yake?" Abba yace "eh an samo shi. Yana wani hotel ya kama daki, Sun rufe masa account din sa dam haka very soon zai nemi gida da kansa. Ja'irin yaro mai tsaurin ido" Mommy tace "irin na ubansa ne ai. Wanne irin tsaurin ido ne ubansa bai yi ba? Zasu zo su saka yaro a gaba wai yayi rashin kunya bayan su babu irin rashin kunyar da ba su yi ba". Gidado da tunda Mommy ta ambaci kalmar aure yaji cikin sa ya juya, yana sane da kallon da Mama take jifansa da shi da nufin ya tashi ya basu guri amma yayi kamar baya ganin ta dan so yake yaji komai a maganar, sai dai kuma sai yaji sun saki maganar sa sun koma maganar cousin dinsa Bassam da yake son khausar ita kuma suna soyayya da Ayaan, wannan ya sa yayi yaji ya bar gidan Auntyn su Hafsat bayan yayi mata rashin kunya, ya koma hotel da zama, yanzu yadda za'a yi ya dawo gida a hukunta shi ake nema. Yana jin Abba yayi waya da Mammy da kuma Uncle Habib yace su zo gidan sa, sannan suka cigaba da hirarrakin su. Sai da Mama taga dai bashi da niyyar fita sannan ta kira sunan sa direct. "Gidado" ya juyo ya kalle ta "tashi ka tafi" babu musu ya mike tare da yi musu sallama ya fita, Sai dai kuma zuciyar sa bugawa take yi sosai, ya tabbatar tunda Mommy ta dage akan maganar auren nan to dole sai anyi shi? Amma kuma da wa? Kar fa aje a sake daura masa igiyar da zai kasa kwance wa bayan ga waccan igiyar har yanzu yana fama da ita. Haka yaje yayi ta shawagi a gari, yasan in yahe gidan sa ma wani takaicin zai tarar, a karshe sai ya tafi gidan Ya Amen ya ci abinci a can suka kuma tattauna akan maganar. Ya gaya masa duk abinda ake ciki, except for abinda ya samu Safiyya, ya dai nuna masa iyayen ta ne suka matsa mata suka hada ta aure da Mukhtar, yanzu kuma da zaman auren yaki yiwuwa sai suka raba. Anan ne Al'ameen ya kuma tabbatar wa da kansa cewa Gidado yana matukar son Safiyya kuma at this stage abu ne mai wahala ya rabu da ita. Dan haka ya yanke shawara a ransa cewa zai je ya gwada bugar cikin Mammy yaji shawarar da suka yanke kuma ya nuna mata abinda ya tahimta da dan uwan nasa, Humaira ta fito sun gaisa, ya karbi Ayman yana yaba wa da yadda yaron yayi girma sosai, a ransa yana fatan ranar da zai ga nasa dan shima, Sai kuma suka vi hirar karatun da Humaira zata fara yi very soon a jami'ar Oxford akan harkar zane zane. Daga nan suka koma hirar Bassam and his drama. Sai da dare yayi sosai sannan ya tashi zai tafi, Humaira tace ya gaishe da Safina, sai yaga sun kalli juna ita da Al'ameen sunyi dariya, ya tambaya "what?" Sai Humaira tayi saurin girgiza kanta "babu komai fa. Ka gaishe ta Please" koma menene bata son ta gaya masa dan ta san tsakanin mata da miji, kar ya gaya masa shi kuma ya gaya wa matar tasa. Sai bayan sun fita sannan Al'ameen ya ke gaya masa ashe wai drama akayi ranar da Safina tazo barkan Ayman. An bata jariri taki karba wai ita bata iya daukan jarirai ba, ai kuwa aunty Amina tana gurin dan haka ta wanke ta tas a gaban mutane, daga baya ta hada da nasiha, shine ta shiga daki ta zauna ita kadai ta ki yiwa kowa magana, Mufida ma da tazo tayi mata magana da niyyar ko zata saki jikinta, har tana janta akan su shiga kitchen suyi girki tare sai tace ita ba zata bata kayan ta da kamshin abinci ba, ai kuwa Mufida taji haushi da kyar su Basma suka hana ta kula ta suyi rigima. Shi dai Muhammad murmushi kawai yake yi, a ransa hangowa yake yi Safiyya ce, yana hango yadda zata shiga kitchen din nan tayi girki, yana hango yadda zata dauki babyn nan ta rungume, yana hango..... Sai da Al'ameen ya taba shi sannan ya lura da murmushin da vake tavi "wato kai murna ma kake yi matar ka bata samu karbuwa a family ba k0? Mugu" Muhammad ya yi dariya kawai ya shiga mota ya tafi amma ya san rashin samun karbuwar Safina a family yana nufin higher chance of samun karbuwar Safiyya. Duk da dare yay amma bai hakura ba sai da ya biya ta gidan su wai ko za'a ce masa wani abu, ya tarar bakin duk sun tafi amma kuma daga Mama har Abba babu wanda yace masa komai. Hakan kuma ya damu zuciyar sa sosai. Gani yake da ace maganar Safiyya suka yi ai da zasu gaya masa ko dan su faranta masa ko? Babu wanda ya kula shi da niyyar faranta masa din sal anar Alhamis, ranar ne Abba yay masa magana casually a harabar gidan su sanda yaxo yake kokarin shiga, "Uhmm Muhammad, maganar da kaji munayi ranar nan da Mommy akan auren da tace ayi maka. Ka amince ayi?" Ya danyi shiru yana kallon sa ya rasa abin cewa, gashi kuma abban a tsaye yake amsa yake jira "aure Abba?" Ya tambaya muryar sa cike da damuwa. Abba ya bata rai "ka zama kurma ne?" Ya girgiza kansa, there is a chance na cewa Safiyya ce sannan kuma akwai chance na cewa ba ita bace ba. Risk ne wannan zai dauka, babban risk. Ya gwada tambaya "Abba aure da wa?" Sai kawai ya ga Abban yayi murmushi sannan ya dan daki kafadar sa kadan yace "some one better than your wife. We will never repeat the mistake we did a baya" ya danji sanyi a ransa, tunda ake maganar Safina sai yau yaji ra'ayin Abba a kanta. Ya san dai koma menene iyayensa ba zasu cutar da shi ba and he trust they will make the best decision for him. A hankali yace "shikenan Abba na amince" Abban ya sake murmushi sannan yace "Allah ya baka ladan biyayya" sai ya juya ya shiga motarsa driver ya ja suka fita. Washegari juma'a ta zagayo amma babu labarin komai. A juma'ar ne kuma bayan yaje masallaci ya dawo Safiyya ta kira shi da tashin hankali a muryarta, tambayar sa kawai tayi yana ina sannan ta katse kiran ba tare da ta ce komal ba, yayi ta kira bata dauka ba, daga nan ta kashe wayar ta ma gabakidaya. Wannan ya tayar da hankalin sa, a niyyar sa in ya koma gida zai dauki motarsa ya tafi ya zaga dangi yayi gaisuwar juma'a kamar adda ya kanyi in ya samu dama. Amma sai ya fasa, yana zuwa motar ya dauka kawai ya fita ba tare da ya ji abinda Safina da ta sha kwalliyar lace take gaya masa ba. Hanyar gidan su Safiyya ya dosa, ko bai shiga ciki ba maybe zai samu wani labari daga gurin mai gadi duk da dai mai gadin shima wani kallo yake yi masa kwana biyun nan. Sai da ya kusa zuwa sannan kiran waya ya shigo masa daga gurin Mama "kana ina? Kazo gida yanzu akwai magana mai muhimmanci" sai yaji a muryarta kamar farin ciki take yi, a yanayin order din da ta bashi kuma kamar laifi ne yayi. Ya rasa menene, amma in dai Mama tayi kira to babu sauran jira. Sawun giwa ya take na rakumi. Kan motar ya juya ya chanja titi zuwa wanda zai kai shi gidan su. Bayan ya shiga sai ya tsaya a harabar gidan yana kallon motocin da suke wajen, kusan duk iyayen sa maza suna nan har da motar uncle dinsa yayan mama dake Kano. Ya fito sai mai gadin su ya karasa da sauri yana watse baki hannun sa rike da goro da alawa yace "ranka ya dade munji abin alkhairi, Allah ya sanya alkhairi ya sa abokan arzikin juna ne ku" gabansa ya fadi, ya kalli fuskar mal gadin ya kuma kalli goron hannun sa sannan yace " meen" sal ya shige cikin gida da sauri. Tun daga waje yake jiwo dariyar iyayen nasa, daga dukkan alama suna cikin nishadi, yana shiga yaji Mama tace "au Amir yaje? Dama yana gari? Yaushe rabon da inga bawan Allahn nan" Abba yace "nima ban san yana gari ba shi yasa ko neman sa banyi ba, sai kawai ganin shi nayi sun zo tare da Sultan. Zan kawo shi gidan nan kuwa insha Allah kafin ya koma Kaduna" Habib yace "ai Sultan ne ya biya sadakj" Mama tace "haba? Ya riga Faruk kenan" Faruk yayi dariya "ya fini baki ai. Kin san yayan nawa ba'a kure shi a magana, Yace lallai wannan aure shine zai biya sadakin sa, dole na hakura na bar masa, Amma ina nan zan bawa ango da amarya gift instead of sadakin da ban samu bayar wa ba". A hankali Muhammad yace "sadakin wa?" Duk suka juyo suna kalion sa, Habib ya mika masa hannu yayin da Mama ta hade rai "baka iya sallama ba?" Uncle Hamza wan Mama yace "in yayi sallamar ma ai ba za kuji ba kuna ta hira, yau dai daya al a daga wa ango kafa kar ayi masa fada" ya karasa maganar yana dariya amma Muhammad kallon sa kawai yake yi. Ya san za"a daura masa aure amma bai san cewa za'a daura ba da sanin sa ba. Ganin duk shi suke kallo dai ya karasa ciki ya zauna a kasa, a tsakiyar su. Uncle Habib ne yayi magana, "Kamar yadda muka shawarta a tsakanin mu, bisa la'akari da dalilai masu yawa sannan kuma da amincewar ka, an daura maka aure Muhammad, da Safiyya Adam Muhammad". Wani murmushi ne ya taso tun daga zuciyar Muhammad har zuwa kan fuskarsa. Wani irin farin ciki yake ji yana lissafin ina ma shi yaro ne ya tashi yayi ta zagaye gidan a guje yana tsalle? Instead sai ya rufe fuskarsa da hannayensa ganin yadda iyayen nasa already suka fara tsokanar sa, "Kaga marar kunya ko? Satin nan gabakidaya a kumbure yayi shi kamar zai fashe amma ji yadda yake murmushi ko kunyar mu baya ji" Abba ya fada da dariya a muryarsa, Daga jin muryasa ka San farin cikin dan na sa ya saka masa farin ciki shima, Faruk yace "ai kuwa dai tushi ya kare, ciwo ya kare, hada akwati a gudu daga gida a je a dauke yar mutane ya kare" ya fada yana dan jan kunnen Gidado kadan cikin tsokana. Gidado ya sake jin sabuwar kunya ta rufe shi. Uncle Habib yace "nauyi kuma ya karu ba. Ni tausayin ka nake ji Gidado. Hada mata biyu musamman masu kusanci da juna irin wanna sannan kuma wadanda kake musu mabanbantan soyayya sosai akwai wahala. Akwai aiki a gaban ka sosai". Daga nan sai suka koma yi masa nasiha akan sauke nauyin iyali da kuma kwatanta adalci. Suka kara nuna masa irin girman da ya same shi da kuma jaddada masa cewa suna tare da shi a duk kan al'amurran sa, duk wata shawara ko wani taimako zasu bashi in dai suna da hali. Sai kuma suka gaya masa cewa idan an jima bayan sallar magrib ya shirya ya kuma nemi abokan sa su raka shi ya gaishe da iyayen Safiyya, daga nan kuma su gano amaryar. Daga nan ya tashi ya shiga dakin sa. Yana rufe kofa ya zarce straight yayi sujjada dan nuna godiyar saga Ubangiji, har sai da hawaye ya kawo cikin idon sa. Ya na dagowa ya cigaba da neman Safiyya a waya, amma still wayarta a kashe. Ya tura mata message ta Whatsapp duk kuwa da yasan ba zata gani yanzu ba. "I am yours, and you are mine. Forever" Daga nan sai ya fada akan gado yana yar dariyar murna, babu abinda yake son gani a lokacin sai fuskarta, ya zata ji? Ya zata yi? Sai kuma ya dauko wayar sa ya kira Ya Amen, yana dauka yace "kai an daura fa" Al'ameen yayi dariya "amma yaron nan ka cika marar kunya wallah, ni ba yayanka bane ba kake ce min wai an daura" Gidado yayi dariya cikin nishadi "watanni ne fa kawai, ko goma basu kai ba" Al'ameen yace "ko kwana goma ne dai na girme ka kuma dole ka bani girma na" Gidado yace "a da kenan, yanzu nine yayan ka in gaya ma" Al'ameen yace "la ila. Da gaske yaron nan ka raina ni fa. Kana gaya min kana da mata biyu ko? Dole Ayaan yaji maganar nan kuwa" suka cigaba da hirarrakin su cikin nishadi, Al'ameen ya gaya masa cewa dama Mammy ta gaya masa maganar auren Gidadon amma Abba ya hana a gaya masa yana son ya gani if he will still do the biyayya without knowing wadda za'a aura masa din. Gidado yayi murmushi kawai suka yi sallama bayan ya sanar masa maganar zuwa gidan su Safiyya in an jima, Sai kuma ya fara lissafin wadanda zai kira a abokan sa, daga baya kawai sai ya fasa yace Al'ameen da sauran kannensu na family sun ishe shi sai abokinsa Usman wanda already ya san Safiyya. A haka ya hada team din sa, Al'ameen, abdulshakur dan aunty Amina, Baffa second child din Uncle Habib, Haidar, sai kuma Usman. Al'ameen ne duk ya gaya musu, ai kuwa nan da nan suka zo gidan suna ta hayaniya da tsokanar Gidado wai ya girmi har iyayensa yanzu, ya zama mai mata biyu. Matan ma sai gasu suna ta zuwa Allah ya sanya alkhairi, gida ya cika kamar ana taron biki, Mama kuwa taji dadin zuwan nasu dan ta samu sun cinye abincin da ta girka wa yan daurin aure dan basu ci ba haka suka bar mata kayanta suka ce sun ci abinci a can. Nan da nan aka cinye abincin tas har sai da aka dora wani. Kowa ya kalli Gidado ssi ya tsokane shi saboda yadda yake washe hakora kamar gonar auduga, kana kallon sa kasan cewa yana cikin farin ciki mai tarin yawa. Sai da suka yi sallar magrib sannan suka fara shirin tafiya gidan su Safiyya, ya shiga toilet yayi wanka, yana fitowa ya ga Kaya akan gadon sa a ajiye, ya san Mama Ce ta ajiye masa, yaji wani sonta yana karuwa a ransa, ya dauki kayan yana dubava, yadi ne fari kal mai laushi a hannu da kyalli a ido, anyi masa dinki itin na zamani da zare off white mai kyalli wanda ya dace da hula da kuma takalmin da ya gani a gefe duk size dinsa, sai karshi suke yi wanda ya san mix ne na turaruka kala kala, Sai kuma dan karamin box dauke da agogon rolex sabo fil, "Mamana" ya fada a hankali yana jin dadi a ransa. Ya saka kayan ya shirya tsaf sannan ya tsaya yana kalion kansa a madubi, ya tuno maganar Safiyya "You will wear white, You will look so good in white" yayi murmushi sannan ya ciro agogon daga cilkin kwalin sa ya saka, Ya ji an danyi gyaran murya daga bayan sa, ya juya yaga mama a tsaye ta jingina da jikin bango, ya danyi kokarin rage murmushin fuskar sa amma sai ya kasa instead sai kawai yayi dariya tare da karasa wa gurin ta da sauri ya rungume ta har da dan daga ta ya raba ta da kasa, ta dan dake shi a katada tana dariya ita ma "ajiye ni kai. Marar kunya*, ¡ajiye ta ta ja dogon hancin sa "kayi kyau sosai Muhammad Gidado" yay kissing goshinta tare da kama hannun ta ya rike a cikin nasa “thank you Mama. I mean thank you for everything” ta gyada kai "Allah ya baka ikon sauke nauyin da ya dora maka, Allah yayi muku albarka gabakidaya", Yace "Ameen" sannan ya wuce ta ya fita. Yana fita matan da suke gurin suka fara rangada guda, shi kuma sai washe baki yake yi. Aka zo akayi ta daukan pictures da shi sai da kyar Abdulshakur ya jashi suka fita. A hanya ma haka suka yi ta raha har suka je gidan, a lokacin ya kara tabbatar wa da cewa bayan Ya Amen da babu wanda ya san alakar da take tsakanin Safiyya da Safina, tunda basu je gidan Daddy ba a lokacin auren Safina, dan haka as far as danginsa are concern Safina yar Katsina ce kamar yadda ta tabbatar musu da kanta. A gidan suka samu tarya daga wani mutum mai cikar kamala da kwarjini wanda daga baya Muhammad ya fahimci shine Uncle Sufyan din da Safiyya ta gaya masa, shi ya shigar da su har wajen Daddy suka gaishe shi, suka same shi tare da uncle Ahmad, shi dai Muhammad yana ta sunkuyar da kai baya son hada ido da Daddy, Daga nan kuma aka dawo dasu parlor suka gaisa da wadda ya gane a matsayin Aunty Hajjo. Sai tace su jira a kawo musu amarya, tun daga nan ya mayar da hankalinsa kan hanyar da yaga ta bi. Yana jin sauran samarin wajen suna ta hirarrakin su amma sam hankalin sa baya kan su, ita kadai yake so ya gani. Sai yaga kamar sun dade da yawa, me suke yi ne wai? A sanda ya dora idonsa a kanta kuwa ji yayi babu wani sauran birbishi na damuwa da ta rage masa a duniya, with Safiyya as his wife, yana maraba da dukkan challenges na rayuwa. Ya lura da kallon da tayi wa Haidar, sannan a take ta fara neman fuskarsa a cikin mutanen gurin. Ya fahimci cewa ganin Haidar da tayi ya saka ta gane da shi a ka daura. Suna hado ido ya mike tsaye tare da bude mata hannayensa, not minding Aunty Hajjo ballantana sauran samarin da suke gurin, ba ta watsa masa kasa a ido ba kuwa ta zo ta shige mazaunin ta, cikin kirjinsa and they had their first halal hug, or maybe he should call it their first hug dan wancan na ranar nan was done a cikin tashin hankali dan haka babu wani feelings a cikin sa. Yana jin hayaniyar mutane amma duk baya jin abinda suke cewa, bugun zuciyar Safiyya kadai yake saurara, tare da dumin jikinta da kuma kamshin da yake tashi daga gare ta. "It is okay. You are okay. Muhammad Gidado is here" ya fada mata a cikin kunnen ta. Ta gado da niyyar kallon fuskarsa yayin da shi kuma yake kallon kasa a kokarin sa na ganin tata fuskar wannan ya saka fuskokin su duka zo dab da juna. Tayi saurin mayar da tata kasa shi ma ya dauke tasa gefe because a yadda yake jin zuciyar sa a kanta anything can happen. Ya lura tunda tazo gurin ake musu hotuna, Aunty Hajjo ta fadi sakon da iyayensu suka bayar sannan ta juya ta tafi ta bar su, daga nan Safiyya ta fara kokarin janye jikin ta daga nasa, maybe sai yanzu ta fara jin kunyar mutanen gurin, ya dan sake ta kadan sannan ya jata suka zauna, tana ta kara lullube jikin ta da katon mayafin da ya kai mata har kasa. Suna zama ya kara riko hannunta yana kokarin leka fuskarta, ta dan harare shi da kumburarrun idanunta, ya fahimci ta dauka ba dashi aka daura ba, Allah kadai ya san yawan kukan da tayi , sai yaji ya hakan yayi masa dadi sosai, it feels so good to be loved by the person you love A hankali yayi mata introducing wadanda suka zo da su, kowa yana tsokanar ta "yau dai munga Safiyya" "daga yau dai mun huta da labarin Safiyya. Daga ina kake Safiyya, ina zaka je Safiyya, me kake yi Safiyya" "Har mafarkin Safiyya fa yake yi, cikin dare zaku ji yana kiran sunan ta" Muhammad yace "ban da sharri kuma. Wannan dai kazafi ne" Abdulshakur yace "a kira Ayaan a tambaye shi ranar nan a UK idan ba sunan ta kake kira mana cikin dare ba". Duk suka yi dariya banda Safiyya da taji kamar zata nutse a gurin., Haka suka yi ta raha suna duke dauken pictures yayin da Esther ta shiga hidimar cika musu gabansu da snacks da drinks, sam ta kasa rufe bakin ta tun da taji abinda ya faru saboda murna. Safiyyah ta lura cewa Abdulshakur yafi kowa surutu da tsokana, yayin da Al'ameen yake zaune kawai yana kalion su yana murmushi, sal jefi jefi zaka ji yayi magana a hankali, Sai da suka fara shiri taliya ne Al'ameen din yazo gurin su yace mata "amarya congratulations, Yanzu dai za'a bar min zucivar dan uwa ta huta" a hankali tace ba tare da ta dago kal ta kalle shi ba "thank you Ya Amen. A gaida Humaira da Mammy" sai yayi murmushi aransa yana jin cewa tabbas dan uwan nasa ya samu chanji. Shi ya hada kan kannen nasa ya kora su waje, ya kuma ce ya bawa Muhammad minti biyu idan bai fito da zasu tafi su barshi sai dai amaryar tasa ta kai shi gida. Suna fita Muhammad ya kara karfin rikon da yayi wa hannun ta. Sannan yayi kokarin daho fuskarta da daya hannun. "Amaryar Muhammad" ta kara sunne kanta gefe tana jin kunyarsa "wai kunya ta kike ji? Ni fa" ta juya fuskarta dayan gefen, da gaske kunyar ta sa take ji musamman yanzu da aka bar su su biyu, Ya danyi dariya "lallai da rabon yau zan kwana a gidan Daddy kenan. Ta yaya zan tafi ba tare da na kalli cikin idon ki ba?" Ya fada yana daga hannun ta da yake cikin nasa ya kai bacin sa tare da hura mata iska a fatar hannun. Tayi kokarin janye hannun amma sai ya kara rikon su tare da fara kissing knuckles din ta one after the other. Ta juyo da sauri ta dora manyan idonta akan sa tace cikin rada "CCTV" yayi saurin sakin hannun yana rarraba ido, sai ta mike da sauri ta bar inda yake tare da cewa "goodnight" yana ta rarraba ido amma da murmushi a fuskarsa yayi mata alamar tazo su je waje da hannun sa. Ta makale kafada, ya hade hannayen sa alamar roko, ta sake makale wuya. Ya kankantar da idonsa a kanta irin kallon da yasan yana saka ta jin kunya sai ta ja mayafin ta ta kara rufe fuskarta. A lokacin aka bude kofa aka fito daga part din Daddy. Duk suka juya suna kallon wadda ta fito din, Mommy ce, fuskar ta jage jage da hawaye, ta kalli Safiyya da tayi saurin sunkuyar da kanta kasa sannan ta kalli Muhammad shima ya janye idonsa daga nata suna adawa, babu wanda ya iya gaisheta a cikin su ballantana yace mata wani abu, ita ma bata ce musu komai ba sai ta wuce ta hau sama. Suka yi shiru gabakidaya babu wanda ya sake magana. Haidar ya dawo yace "Wallahi Ya Amen yace zamu tafi mu barka" Gidado ya gyada kai, kafin yace komai Safiyya ta juya ta bi hanyar da ya ga ta fito daga ciki. Haka ya tashi ya fita, bai ji dadin ganin hawaye a idon Mommy ba amma shi kam yau babu abinda zai saka wa farin cikin sa shamaki, Suka shiga motocin da suka zo a cikin su sannan suka fita cikin nishadi kamar yadda suka shigo. Daddy... One week ago.... Ya dago kaga kai yana kalion bakon nasa wanda shi da kansa ya ce a shigo da shi har cikin dakin sa. Suna hada ido sai yaga yanayin bakon nasa ya chanja gabaki daya, lokaci daya yayi wani irin sanyi wanda da bai shigo da shi ba. Maybe kuma hakan yana da dangantaka ne da yanayin rashin lafiyar da yake ciki da kuma injinan da suke zagaye da shi. Yayi masa maraba tare da nuna masa kujera "bismillah". Abba ya zauna yana cigaba da kare wa dakin kallo wanda ya fi masa kama da dakin asibiti. Daddy ya danyi murmushi yace "forgive all the medical tarkace, Safiyya ce duk ta cika min daki da shirgi, ni kuwa na san duk yawan machines din da zata siya lokaci yana cika zan tafi"., "Me yake damunka?" Abba ya tambaya da Hausar sa mai accent din fulani irin na Muhammad Gidado, Daddy yace "ALS" sai Abba ya cigaba da kalion sa da rashin fahimta, Daddy ace "neuromuscular disease ne da yake paralysing muscle, thereby restricting movements. Ba zan cika ka da medical jargons ba amma already na wuce time din da doctors suka yi tunanin ba zan kai ba" Abba ya girgiza kansa "ba su suke bada rai ba. Ba kuma su zasu dauka ba" Daddy ya gyada kai "you are right, I am a living testimony. But I am sure ba wai kazo dan jin labarin rashin lafiya ta ba ko? What brings you to me?" Abba ya danyi shiru yana tattaro tunanin sa waje daya, ganin Daddy ya taba zuciyar sa sosai. Muhammad bai taba gaya masa cewa bashi da lafiya ba. Ya danyi gyaran murya sannan yace "hmmm.... I don't know ko kasan ni waye" Daddy yace "baban Muhammad ne, mijin Safina. Kuna kama sosaj" Abba ya dan yi murmushi tare da shafa gefen fuskarsa sai kuma yace "haka ne. Amma ba maganar Safina bace ta kawo ni. Nazo ne farko ina so inji ko kana da masaniya akan alakar da take tsakanin Muhammad da Safiyya?". Daddy ya danyi shiru kamar mai tunani sannan yace "na jima da sanin cewa akwai wani yaro da Safiyya take so, in fact, tayi ta kokarin ganin cewa ta kawo min shi ya shigar da maganar auren ta ni kuma na hana ta saboda burin da na dora akan ganin tayi karatu mai zurfi, saboda wasu dalilal nawa. Daga baya kaddara ta gifta wadda tayi sanadiyyar rabuwar su. Amma ban san cewa shine Muhammad din da kannen mahaifin Safina suka daura mata aure da shi ba sai kwanan nan. So your answer is yes, na sani". Abba ya danyi shiru yana digesting wanna amsar sannan kuma sai ya sake yin wata tambayar "and what do you think about their relationship. Menene matsayar ka akai" Daddy yace "nace wa Safiyya no. Na gaya mata cewa ba zan aura mata shi ba duk kuwa da a fahimci soyayyar da take yi masa, na hana ta auren sa saboda kasancewar sa mijin Safina. I don't know ko kasan relationship din da yake tsakani na da mahaifiyar Safina?" Abba ya gyada kai "na sani. Babu wanda ya gaya mana hakan a danginta, amma mun binciko hakan sanda muna bincike akan auren ta". Daddy yace "good. I raised her like my daughter. Ba zan ce na so ta kamar yadda nake son Safiyya ba but I did my best. Sun tashi kamar sisters. Wannan ne abinda ya kara bata min rai sanda na hana Saliyya alaka da Muhammad amma taki jin magana ta ta cigaba da ganin sa behind my back. Na tambaye ta kuma dalili ta kiyi min cikakken bayani illa cewa tana son sa. I got scared, I am a sick father unable to guide and protect his only daughter, Wannan ya saka na saka cctv a dukkan bangarorin da suke gidan nan except for bedrooms. Na saka ne dan ita. Dan in san duk wani move dinta in kuma yi kokarin discharging fatherly duties dina. She told me cewa zata rabu da Muhammad kamar yadda na bukata tunda ta ga raina baya so. She invited him in, suka zauna, and they had this conversation" ya fada yana mika wa Abba wayar da take hannun sa. Ya kara da cewa "ka kalla tun daga farko har karshe sannan sai kai ka gaya min abinda kake tunani a game da alakar ta su" Abba ya taso ya karba, fuskar Muhammad din sa ya gani da ta yarinyar da ya jima da sanin sunan ta amma sai yau ya fara ganin tata fuskar. Daddy ya kara da cewa "duk abinda zaka ji ta fada, gaskiya ne, abinda ya faru da ita kenan". Abba yayi shiru yana sauraron maganganun Muhammad dana Safiyya da suke fitowa tas ta jikin speaker wayar. Sanda ya gama gabakidaya a razane yake. Hankalin sa ya kai makura wajen tashi. "Ina yake?" Ya tambaya "shi Mukhtar din ina yake? Da gaske kun barshi? Kun kyale shi?" Daddy yace "da gaske mun barshi da Allah. Mun kyale shi shida Allah, Muna nan muna jira. A haka ma da muka rufe maganar Safiyya is about to lose the person she loves very much, me kake tunanin zai faru da ita idan muka fito da maganar? Bata aikata laifin komai ba but most people will run away from hada zuriyar su da ita....." Abba yace "then most people da kake magana a kai a jahilai. Wannan abu ne da jahilai zasu aikata, Kuma alhamdulillah Alhaji Adam, dani da iyali na bama cikin jahilai, kamar yadda na tabbatar kaji a cikin maganganun Muhammad". Daddy ya dago kai yana kallon sa yace "me kake nufi?...." Abba yace "ina nufin ina nemawa dana Muhammad auren Safiyya a gurin ka. In dai har kana ganin zaka iya bashi ita duk kuwa da alakar da take tsakanin ku da matar sa ta yanzu". Daddy yayi shiru yana kallon sa sannan ya maimaita masa maganar da ya tabbatar yaji a cikin hirar su Safiyya "Safiyya ta na da da, wanda ta haifa ba tare da aure ba. Ka tabbatar a haka kake so ka aura wa danka ita?" Abba ya gyara zama yace "na tabbatar, dalili na na farko shine ina da ya, kwanan nan na aurar da ita, na tabbatar kuma cewa har yau har gobe bata wuce kaddarar da ta fada kan Safiyya ta fada mata ba. Babu wani a cikin mu da ya isa ya wuce jarabawar sa. Dalili na biyu shine ban taba ganin soyayya irin wannan da na gani a tsakanin wadannan yaran ba, zan iya cewa daga ni har kai munyi kuskuren barin su suyi zurfi irin wannan, Allah ne ya kare mana su but they are too close. Yarinyar nan ita ce farin cikin Muhammad, a matsayi na kuma na mahaifin sa zan yi iyakacin kokarin gain na samar masa farin ciki in all the halal ways. Tambaya ta anan ita ce, zaka iya aura wa yarka mijin step sister din ta?" Daddy yayi shiru yana dan juyi akan wheelchair dinsa, fuskarsa duke da murmushi kamar mai tunani, sai kuma yace "ni uba ne. And it is very okay for parents to be selfish sometimes when it comes to their kids. Parents have to be selfish sometimes" Abba yace shima yana murmushi "not sometimes, parents are selfish all the times when it comes to their kids. Haka din kuma dai da ne. As long as their selfishness bai zamo shiga iyakar ubangiji ko danne hakkin wani ba. Then it is okay 1 am ready to be selfish if you are" Daddy ya mika masa hannu suka yi musa biha, fuskokin su duk da murmushi, wani bond mai karfi yana creating kansa a tsakanin su. Abba yace "abu daya ne ya saka ba xan daura wa Muhammad aure da Safiyya a yanzu ba. Shine mahaifiyata da yan uwa na. Bama taba yanke wani babban hukunci ba tare da mun sanar wa da junan mu ba. Zan je in same su muyi magana, zan gaya musu iyakacin abinda nake ganin ya kamata su sani. Zamu tsayar da rana cikin satin nan zamu dawo a daura musu aure" Bayan sun rabi Daddy ya kira Sufyan ya sanar masa, sannan ya kira Ahmad shima ya sanar masa da abinda ake ciki, dukkan su sunyi murna kuma a take Sufyan ya shirya suka taho Nigeria shida iyalinsa dan yana son ayi komai da su, musamman bayan yayi magana da Hajjo kuma ta tabbatar masa da cewa ta san mahaifiyar Muhammad din kuma sunyi maganar Safiyya da ita few days ago. Dasu akayi shirin komai, Daddy ya roke su akan kar su fada wa kowa har sai maganar ta tabbata, baya son attention din mutane akan maganar, bayan son attention din mutane akan Safiyya. Bai gayawa Mommy ba saboda bash da tabbas din yadda zata vi reacting to maganar. Ya san kuma in dal ta sani to sai Safina ta sani, duk da yasan hakan ba zai hana faruwar auren ba dan babu mai saka wa ko hana wa a cikin su amma ya san hakan zai iya janyo unwanted attention din da baya so. Ko a ransa bai ji cewa yayi wa Safina ba dai dai ba musamman bayan zargin da yake yi na cewa ita tayi wa Safiyya kwacen saurayi, plus mugayen karerayin da ta fada akan Safiyya dan ta bata ta a grin Muhammad. Amma kuma a ransa yasan cewa baiyi wa Sa'adatu dai dai ba na kin fada mata da yayi. Sai dai ita mutum ce da ba'a gane kanta, shi kuma a yanzu da yake gab da cimma burin sa na gyara kurakuren da yayi akan Safiyya, baya jin zai iya daukan risk. Present day….. Bayan angwayen sun fita daga gabansa sun koma babban falon gidan, sai Daddy ya dauki waya ya kira number din Mommy kamar yadda ya shirya zai yi. Ya gaya mata ta same shi a dakin sa amma ta biyo ta barandar sama dan akwai baki a falon kasa, sai da ta zo ta zauna sannan yace mata yana zuwa. So yake kawai ya ga tuskar Safiyya a lokacin da taga Muhammad a matsayin angon ta. Sai da ya gani din kuwa, and murmushin da ya gani a kan fuskar ta was worth all the risks he took to put it there. She said "thank you" to him, he gave her a thumbs up sannan ya koma cikin dakin sa inda Mommy take zaune tana jiran sa. Ya shiga ya rufe kofa sannan ya zauna suna kallon juna na was seconds sannan tace "kace inzo zamuyi magana. Kace kuma akwai baki, bayan dazu babu irin tambayar da banyi maka ba akan bakin da za'a yi kaki gaya min su waye. Su waye bakin? Wacce magana zamuyi?" Ya cigaba da zama a inda yake, a ransa yayi hakan ne dan kar tace zata fita wajen bakin ta basu kunya a cikin surukai. Ya sauke ajiyar zuciya yace "dazu da yamma. Na daura auren Safiyya da Muhammad". Farko zama tayi kawai tana kallon sa kamar bata fahimci abinda yace ba, sai kuma da tsananin mamaki tace "what? Adam me kake cewa ne haka? Wanne Muhammad din? Mijin Safina?" Ya gyada kansa a hankali still idon sa a kanta yana kokarin studying dinta. Shi da whatever zata yi baya son ta fita falon nan, Amma sai yaga ta cigaba da yin shiru tana kallon sa, sai kuma a hankali hawaye suka fara bin ion ta. Ya fara driving kujerar sa zuwa gare ta sai ta daga masa hannu. "Don't! Kar kazo nan. Kar ka gaya min komai. Bana son jin komai. Ka bani hanya in wuce. Kwana daya ba zan kara a gidan ka ba. Yau nayi nadamar shekarun da na bata tate da kai. Dama na riga na san cewa kai mutum ne mai son kanka amma ban tana zaton ka kai haka ba sai yau" sai kuma ta koma ta zauna tare da rushewa da kuka mai kona zuciya. Bai ce komai din ba ya cigaba da zama a bakin kofa. Sai da tayi mai isarta sannan ta dago tana kallon sa ta sake maimaita abinda ya gaya mata, maybe dan ta kara tabbatar wa ba wai ji ne bata yi daidai ba. "Mijin Safina fa kace ka daura wa aure da Safiyya. Mijin Safina fa. Kana cikin hayyacin ka kuwa?" A hankali yace "yana sonta, kuma tana son shi. Sannan ba haramun bane ba" ta girgiza kai cikin dacin zuciya "ita kuma duk abinda take so Sal ta samu kenan, Ko da kuwa abin ba nata bane ba na wata ne sal ka kwace ka bata kenan. Wannan wanne irin son kai ne?" Sai ya maimaita mata maganar da suka yi da Abba. "Parents are at times selfish when it comes to their kids. And thst is okay. In dai har ba'a shiga hakkin wani ba". Tace "hakki? Shiga hakki fa kake magana akai. You just destroyed Safina's marriage just so that Safiyya can get married to mijin Safina da ta gani tana so. Kuma kake min maganar shiga hakki?" Yay driving kujerar sa zuwa inda take yace cikin sassanyar murya "kin taba tambayar Safina yadda suka had da Muhammad?" Ta goge hawayen fuskarta "menene hadin wannan da auren da ka hada?" Yace "it has everything to do with it. Kin taba tambayar ta?" Yadda taga ya sassauto da muryar sa ya saka ta baci amsa duk kuwa da wani irin haushin sa da take ji daga shi har yar lelen yar tasa. "Na tambaye ta tunda ni na damu da ita, kai da baka dauke ta yar ka ba ai ko maganar ba ka yi mata ba. Da tace min friend request ya tura mata a social media sai suka zama abokai daga baya suka fara soyayya, sai da incident din ranar dinner dinta ya faru iyayensa suka zo nan sai na fahimci akwai wata a kasa, dana sake tambayar ta sai ta gaya min cewa a social media taga hoton sa ta fara son sa, sai tayi cigiyar ko akwai wanda ya san shi ya hada su, shine kanwar sa ta hada su" Daddy yayi ajiyar zuciya yace "bani da tabbas din gaskiyar haka ko rashin gaskiyar hakan. Abinda nake da tabbas a kan sa shine Muhammad shine yaron da Safiyya ta saka kika yi min maganar sa shekaru biyu da suka wuce, shine yaron da suke tare a garin nan sanda tana karatu, shine yaron da muka dauka shi yayi mata ciki ita kuma ta ki gaya mana waye shi saboda ta san ba shi bane ba. Wannan dalilin ne ya saka ta yanke jiki ta fadi ranar da aka dura wa Muhammad aure da Safina. Ina kyautata zaton hoton auren ta gani a waya. He was Safiyya's before he became Safina's. Dan baka ba abin Safina na kwace na bawa Safiyya ba. Yes, I am selfish, amma ban shiga hakkin Safina ba". Tayi shiru tana tunani, and she remembered wani dare a Berlin da Safiyya ta farka tana ihun kiran sunan Muhammad. Shine Muhammad din? Ta dago kai tana kallon Adam, not knowing what to say or feel, Sai tace "tun yaushe kasan hakan? And you never think of telling me? Saboda me? Saboda kana ganin bam isa ba dan bani na haifi Saliyya ba? Saboda kana ganin ban isa kayi shawara dani a duk al'amurra da suka shafi Safiyya ba? Ba ka taba yarda da ni akan yarinyar nan ba and it hurts me more than anything. Ba ka taba gaya min komai da ya shafe ta, ita ma kuma ba ta gaya min. Me yasa a matsayi na na uwar ta tun da taga Muhammad din ba zata same ni ta gaya min ba?" Yayi shiru yana kallon ta, and she truly looked hurt, da alama abin yayi mata ciwo sosai. Jin bai ce komai ba ta cigaba da amayar da abinda yake ranta "misali maganar kayan Safiya, wai ace ka ajiye kaya a gidan nan kusan shekaru ashirin amma minda nake matar gidan ban san suna cikin gidan ba. Sannan yaron nan da ta haifa, da ga kai har ita babu wanda yayi min maganar yaron nan sai a gidan biki na ganshi" Sai yace "Safiyya have her own reasons da yasa ba ta gaya miki magana, Ni ma kuma ina da nawa daban. This may hurt you amma na tabbatar kin san gaskiya ne. Kina da son abin duniya Sa'adatu. Kina da son kudi sosai ta yadda har ba kya iya boyewa. Ni da ke duk munsan dan su kika aure ni. Safiya have told me a lot about son kudin ku jokingly dan haka tun sanda na aure ki na san halin ki" tayi shiru ranta yana kara baci akan abinda yace, amma kuma a kasan ran nata ta sam gaskiya ce. A bitter truth. Ya cigaba "it is hard to know where a person stands with people like you. Ba'a gane soyayyar ku ta gaskiya ko akasin hakan. Yanzu misali tun ranar da na gaya miki cewa almost all of my wealth belongs to Safiyya sai kika tattara ni kika watsar, duk wata kulawa da da sanda nake hidimar fita dake kasashen duniya for vacations kike yi min yanzu kin daina. Ita dukiya tana da santsi ko da a gurin wanda bai damu da ita bane ba, yo ina ga wanda yake son ta ido rufe? Dan me ba zan ke boye miki abubuwa ba?". Ta sunkuyar da kanta kasa hawaye suna cigaba da zuba a idonta tace "na so Safiya, in kuma son Safiyya" yace "sannan kuma kina son dukiyar su. And it is okay kamar yadda na fada wa Safiyya sanda ina kokarin convincing dinta ta auri Mustapha, Life is mostly trade by batter. Maganar Safiyya kuma dalilin da yasa ba ta gaya miki gaskiyar abubuwan da suka shafe ta shine saboda mentally ta riga ta saka a ranta cewa ko ta gaya miki ba zaki yarda ba" ta dago kai tace "saboda me? Ita tace maka haka?" Ya girgiza kai, "Kwanan nan na fahimci hakan. Saboda tun suna yara in ta gaya miki magana ba kya dauka kin fi yarda da abinda Safina tace miki a kanta" ta bude ido "kuma kace ba ita ta gaya maka ba" yace "ba ita ta gaya min ba. Maganar naji suna vi ita da Mustapha, bai musa ba kuma, kamar yadda bai musa cewa yana shiga dakinta for years yana neman ta ba". Wata zabura Mommy tayi ta tashi saura kadan ta fadi sai ta fada kan kujera, ya zagayo tare da mika mata hannu duk da ba iya taimaka matan zai yi ba. Nan take muryar ta ta cigaba da rawa, hawayen idon ta ya dawo,. Yace "wannan pain din shi na gudar miki shi yasa na kasa fada miki. Yanxu ma ina gaya miki ne kawai dan ki fahimci maganar sosai kar ki fahimce ta a bai bai ki yi abinda zai raba min kan iyali" tace "duk wanda ya gaya maka wannan maganar karya yake yi. Ko safiyyan ce ta gaya maka karya take yi masa, so take kawai ka kore shi dan bata son auren sa. Wallahi sharri take yi masa" ya girgiza kai yana dan murmushi "kamar yadda na gaya miki, parents are all selfish when it comes to their kids. Already har kin goyi bayan sa, Kuma again kamar yadda na gaya miki, babu wanda ya gaya min, ni na gansu suna maganar, na kuma ji duk abinda suke cewa" ya dauko wayarsa "kina so ki gani?" Ta bishi da kallo kawai ta kasa cewa komai sai yace "na saka cctv a gidan nan ba tare da kowa ya sani ba, saboda rashin lafiya tayi limiting yadda zan saka ido tare da kula da iyali na, Ta haka na gansu suna maganar, basu san ina jin su kuma ina ganin su ba, so it's pure truth. Ya jima yana so ya lalata ta, innkika je dakin ta kika duba zaki tarar da wukar da ta ajiye saboda tayi masa barazana dan ya shigar mata din, wanna shine dalilin kiyayyar ta gare shi. Wannan shine dalilin kiyayyar ta ga auren sa. Wannan kuma shine dalilin da ya sa na kore shi", Ya fada yana cigaba da mika mata wayar. Bata karba ba sai ta kife fuskarta a jikin kujera tana kukan takaicin halin yayan ta, ya dora hannun sa a bayan ta cikin shigar lallashi yace "kiyi hakuri, Babu iyayen da suke perfect. Ni da ke duk munyi mistakes gurin raising yayan mu. We should have separate Mustapha from Safiyya tun sa da suka balaga dan ba muharraman juna bane ba. We should have listened more to their small complains and act on them, we should have investigate magana idan suka gaya mana ba wai mu yarda da su blindly be. Amma lokaci bai kure ba, we are still alive and we can fix their lives, wannan shine abinda nayi ga Safiyya. The biggest mistake I made a rayuwar ta shine not listening to her sanda ta ce ta samu wanda take so zata aura. Da tana gidan mijinta da maybe duk abinda ya faru da ita bai faru ba". Ta dago kanta "yanzu to ni yaya zanyi, ta ina zan fara? Me zanyi akan Safina?" Yace "that is where maganar investigate ta shigo ciki. We will investigate, mu tace karya daga cikin gaskiya a maganganun da Safina ta fada yadda mu zamu samu fahimtar maganar sosai. Sauran kuma ya rage na mijin ta. Amma ni in kika tambaye ni zan ce miki chances are very high that Safina ta san Muhammad shine saurayin Safiyya. A tunani na hoton da tayi talla dashi a social media a wayar Safiyya ta dauka" Mommy ta fara girgiza kanta sai ya sake yin murmushi yace "kamar yadda na gaya miki, parents are naturally selfish when it comes to their kids" Daga waje yaji karar bude gate sannan yaji ana shiga motoci, ya san bakin ne zasu tati, Sai ya sauke ajiyar zuciya ya tuka kujerar sa zuwa wajen kararrawar kiran nurse dinsa, it has been a long day, yana bukatar yayi bacci kuma, Ganin haka ya sa Mommy ta mike, still not knowing what to think or do. Zuciyar ta tana yi mata zafi, abubuwan sun cunkushe mata a kanta, bata san menene zata dauka menene ba zata dauka ba. Bata tashi fahimtar zurfin bacin ranta ba sai da ta fita falo tayi mugun gain Safiyya da Muhammad, ba tare da tace musu komai ba ta wuce su zuwa sama sannan a tsaya a bakin window tana kallon motocin da suka fita daga gidan. Sai dai motocin ba su jima ta fita ba wata taxi ta tsaya a kofar gidan sannan wata mata ta fito daga ciki, ssi da ta shigo gate sannan Mommy ta gane ta Safina, duk ta fita daga hayyacin ta kamar mahaukaciya sabon kamu. Da sauri Mommy ta fito daga dakin ta sa sauko daga stairs din a dai dai lokacin da Safina ta shigo falon, idanunta jage jage da hawaye. "Mommy zuciya ta zata fashe, Mommy zan mutu, Wayyo Allah na., Wayyo Muhammad. Wayyo Abba na", Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Satiyya❤️‍🩹 Episode Sixty Two: Unloved Not Edited… "Mommy zuciya ta zata fashe, Mommy zan mutu. Wayyo Allah na. Wayyo Muhammad. Wayyo Abba na". Kuka da hun Safina ya cika gidan gabakidaya. Babu wanda bai ii ba har Safiyya da Aunty Hajjo da suke dakin safiyyan. Suka fito da sauri a lokacin da Mommy ta fito ita ma ta sauka kasa da sauri. Sai suka tsaya akan barandar suna kallon yadda Safina ta zube a tsakiyar falon tana wani irin kuka. "Yaya za'a yi min haka a gidan nan. Ta yaya za'a aurawa Safiyya mijina. Mommy how can vou let them do this to me? Wannan wanne irin son kai ne? Wannan wanne irin rashin adalci ne? Ba zan iya ganin ta da mijina ba, Mutuwa zanyi Mommy". Mommy ta karasa gurin da sauri kamar zata kifa, ta saka hannu daya ta kamo ta ta dago ta sannan ta sauke mata wani gigitaccen mari da dayan hannun, Kartin marin ya saka Satina ta sake kifewa a wajen tare da rushewa da wani sabon kukan. Mommy ta sake kamo ta ta kara sauke mata wani a dayan side din fuskar. Nan da nan fuskarta ta kara ja saboda kuka da kuma zafin marukan, Mommy ta saka kafa ta dake ta, hakan yasa ita kuma tayi baya saira kadan ta fadi Aunty Hajjo da tayi saurin saukowa ta rike ta. "Sa'adatu menene hakan? Zaki ji mata ciwo ki jiwa kanki ciwo kema" Mommy ta nuna Safina cikin dacin zuciya "ba mutuwa taxe zata yi ba? Gwara in kashe ta da hannu na akan ta mutu saboda namijin da bai damu da ita ba. Gwara in kashe ta da hannuna akan bakin cikin da take kunsa min akan da baya son ta. Namijin da ta lalata alakar ta da yar uwarta saboda shi" ta fada tare da kwacewa daga hannun Aunty Hajjo ta koma ta damki kunnuwan Safina duk biyun ta sske dago ta zaune, Safina tayi karar azaba tana jin kamar zsta ski fitsari a wando, Mommy tace "dan ubanki ki gaya min gaskiya, kin san saurayin ta ne kafin ki kai masa tallan kanki ko baki sani ba? Shi yasa kika tafi da shi Katsina dan ba kya son ya ga Daddy ya gane? Dan ubanki ba zak| gaya min gaskiya ba?" Aunty Hajjo ta banbare hannun Mommy daga kunnuwan Safina, ita kuma tayi sauri ta rike kunnuwan tana jin kamar Mommy ta cire masa su, ta ma daina kukan yanzu dan abinda take ji a zuciyar ta yati karfin kuka, the last person da taje tunanin zata goya mata baya ta debi kasa ta watsa a idanunta. Wani irin bakin ciki take ji da take gain gwara mutuwa akan sa. Yanzu ne ta kara tabbatar wa cewa kaf duniya babu wanda yake son sa, me ya rage mata to? Me zata zauna tayi a duniyar kuma? People have always love Safiyya more…... Tun suna yara, hatta Mommyn ta ma da ba ita ta haife ta ba gani take yi kamar tafi son Safiyya a kanta. A makaranta ma anfi son Safiyya duk kuwa da cewa tafi Safiyyan hakuri da biyayya, Safiyya taurin kai da tsaurin ido da rashin kunya da shegen iyayi da manyance wanda Safina take finding very annoying amma kuma still an fi son Safiyya. Ko kawa tayi to kuwa in dai har ta hada su da Safiyya sai ta ga kawar ta koma ta zama kawar Safiyya ita ta koma second choice. Ballantana Daddy da baya boyewa. Daddy bai taba hada Safiyya da kowa ko komai a rayuwar sa ba. And that made her crave for a father's love duk kuwa da cewa yana sauke musu dukkan hakkokin uba amma tana kwadayin soyayyar da yake yiwa Satiyya. Sail dai in Safiyya bata ambata ko kuma ta nuna tana son abu ba to sai ya samo mata shi sai dai in har abin mai cutar wane. Wani lokacin Safina har mamakin audacity din Safiyya take yi, tana kuma jin haushin iyayen nasu akan biye mata akan duk abinda ranta yake so, tana ganin bata ta suke yi. A hankali ta fara kallon Safiyya a matsayin marar tarbiyya, ta kuma fara ganin kanta a matsayin ita ce mai tarbiyya. And she started wanting people to believe that. Tun daga lokacin ta fara jingina duk wani abu marar kyau zuwa da Safiyya, duk wani abu mai kyau kuma zuwa gare ta. Like, as the good girl that she is, she deserves everything good. Mentally kuma ta saka a ra ta cewa Safiyya will end up bad, tunda dai tarbiyya bata ishe ta ba. Wannan ya sa duk wani laifi da akayi automatically zata jingina shi ga Safiyya. Ko menene gani take yi tabbas Safiyya zata iya aikata shi tunda bata da tarbiyya ba kuma ta tsoron kowa, to tsoron me zata ji tunda ba hukuntata za'a yi ba? lya kaci Mommy tayi ta mata fada idan Safina tace tayi wani abu, shima fadan daga baya saboda rashin tarbiyya in Mommy tana yi mata shi sai ta saka hannu ta toshe kunnuwanta ma'ana ba ma zsta j ba ballantana tayi aiki da shi, ta kuma rufe idonta ma'ana ba ma zata gani ba ballantana abin ya dame ta. Wanna ba karamin bata ran Safina yake yi ba, tana ganin Safiyya ta raina mata uwa, wato ta mayar da ita mahaukaciya ko kuma karyar da zata yi ta haushin ta ita kadai. Dan haka ta cigaba da jiran that bad thing da tasan tabbas tana nan tahowa kan bad girl like Safiyya. And it eventually happened. Rana daya Mustapha da Daddy suka dawo da ita daga Abuja, Mustapha kuma ya sanar musu ita da Mommy cewa Safiyya ta fara shaye shaye, wannan maganar ta taba zuciyar Mommy sosai, it kuma Safina ba zata ce tayi mamakin hakan ba dan dama ita ta san karshen alawa kasa, duk kuwa wanda ya sai rariya ya san zata zubar da ruwa, a ranta kuma sai ta saka kan cewa downfall din Safiyya ne ya fara, and more is coming. Kamar kuma ta fada da bakin Mala"iku sai gashi ta shiga dakin Safiyya ranar nan ta ganta kwance male male a cikin jini da kuma kwalin maganin zubar da ciki a gee. Lokaci daya ta fahimci abinda ya faru, Safiyya cikin shege tayi kuma ta zubar da shi. ita ta fada wa iyayen su, and da kyar ta iya containing dadin da ya cika zuciyar ta sanda ta ga Daddy ya dauki belt yana tafka wa Safiyya, she deserves that, the spoilt little bitch. And a ranta ta sake cewa kadan ma kenan, More are coming. A ranta tayi niyyar sanarwa da duk kawayensu da suke bawa Safiyya more importance than her, dan su san cewa Safiyya is the bad one ita kuma ita ce ta gari, amma sai Mommy ta kira su har daki uta da Mustapha ta ja musu kunne da manya manyan kalmomi akan duk wanda a cikin su ya fitar da maganar waje to babu ita babu shi har abada. Ta kuma sake sealing bakunan su ta hanyar kara tabbatar musu da kudurin ta na aura wa Mustapha Safiyya. "Dan haka in kun fitar da maganar ma nan gaba ku zata shafa idan akayi auren" "amma Mommy in akayi haka ba'a yiwa yaya Mustapha adalci ba, wanna lalatacciyar yarinyar za'a aura masa? Yarinyar da take shaye shaye ga kuma cikin shege tayi sai kuma a makala masa ita?" Mommy ta doke bakinta da bayan hannun ta "kar in sake ji. Wallahi Safina ki fita daga ido na, Kar in sake jin kin fadi wadannan mugayen kalaman a kan yaruwarki. Kaddara ce ta same ta kuma babu wanda ya wuce wannan kaddarar" Sai Safina ta juyar da kai tana hawaye. Me yasa su basa ganin abinda take gani ne? Me yasa idon su yake rufewa akan Safiyya ne? Amma kuma dole tayi shiru din, dan ta fahimci Mommy da gaske take sai ta bala'in bata mata rai in dai maganar nan ta fita tunda daga alama Mustapha ya karbi maganar auren kuma ba zai fitar da maganar ba. Dan haka ana jin maganar a waje Mommy zata gane ita ce. Amma kuma ta wani bangaren sai taji dadin maganar auren Safiyya da Mustapha. Hakan yana nufin a step toward cikar muradin zuciyarta. Sai kuma ta samu kanta da murmushi bayan ta goge hawayen fuskarta. Muhammad will soon be hers insha Allah. Tun hutun Safiyya na farko bayan ta fara MD University ta zo wa da Safina labarin Muhammad. "Nayi saurayi Safina" ta fada boldly kamar yadda ta saba yin maganar ta direct, ko tayi maka dadi ko akasin haka kai ka sani. "Malam Muhammadu. Malami ne a MD" Safina tayi dariya, sunan sounds like sunan tsohon lecturer mai fama da tsohuwar mota. "Allah ya shire ki Safiyya. Ke kuma duk iyayin nan naki akan lecturer zaki kare?" Safiya tayi murmushi "ina son sa a haka. Shima kuma yana so na sosai. Love is all that matters" ta fada tana juyi akan gado dramatically. Safina ta girgiza kai kawai a ranta tana jin downfall din Safiyya yazo finally dan in dai tace tana son abu to da wahala idan bata samu ba, she will end up with tsohon lecturer maybe ma mai mata da yaya, watakila ma ya kusa retire. Yayin da ita kuma Safina zata samu prince charming dinta. Ta rufe ido tana lissafo kamannin sa a ranta, dogo, fari tas, masculine, kyakkyawan gaske with a true red lips that she so much likes. Mai matukar sonta kamar ya chine ta. Very romantic wanda zai ke kashe ta da kalamai da tarairaya da kulawa. And also very rich, mai hawa manyan motoci da saka suturu masu dan karen tsada. Tayi murmushi, Safiyya can go with her Malam Muhammadu. Ita kam ta riga ta gama picturing irin mijin da take so and they will live happily ever after, while Safiyya's marriage will probably crumble saboda rashin tarbiyyar ta. Wanna buri da ta dora akan irin kalar mijin da take so shi ya hana ta kula samari, samari da yawa suna nuna suna sonta, duk da dai most of them ba sa iya fuska, amma kat cikin su babu wanda yayi fitting dream husband dinta, Shiga jami'ar da tayi ita ma anan kano ya kara mata yawan masu cewa suna sonta, ciki kuwa ranar nan har da wani malamin makarantar ta su da har ya bata dariya ma, ta yaya ma zata kula shi? Sai kace wata Safiyya. So take ta kere Safiyya a miji kamar yadda ita kuma ta kere ta a komai banda tarbiyya. A haka har Safiyya ta sake dawowa next hutu, a lokacin ne take gaya mata already "malam Muhammadu" ya fara yi mata maganar aure. "Kin san kuma Daddy ya ja min kunne akan yin soyayya, tsoro na ke j'"' sai Safina tayi dariya "ke ce fa Safiyya, da kin yi wa Daddy kuka shikenan zai aura miki Malam Muhammadun ki" amma sai Safiyya ta girgiza kai "no, ba zai yi ba. He is very serious about it". Wannan kuma ya saka Safina wondering why? Me yasa Daddy zai hana Safiyya samari amma ita bai ce mata komai akan hakan ba? Sai kuma ta samu amsa dinta a ranar 20th birthday din Safiyya. Ranar da Daddy ya tara su tare da wadansu mutane da suka sha suits, ya shirya musu tatsuniyar cewa kusan duk abinda ya mallaka mallakin Safiyya ne. Ranar yadda Safina taga rana haka taga dare. How? Why? Ta yaya Safiyya zata samu wanna abin, she do not deserve it. Ita ma kamar Mommy, daga farko ta dauka son zuciya ne kawai ya saka daddyn fadar haka dan ya san ya fara rashin lafiyar da bata da magani kuma in ya mutu gadon Safiyya bashi da yawa, sauran duk na Mommy ne da twins, amma daga baya ita ma sai ta fahimci da gasje maganar haka take. Abin ya kona mata zuciya sosai. Sannan ya dasa mata wani abu a zuciyarta game da Safiyya bayan kiyayya. Hassada. Bata tashi kara raina kanta ba sai da ta fahimci '"malam Muhammadu" fa is not someone she pictured him to be. Ba tsoho bane ba, and he is far from being poor. Ba wai ganin shi tayi ba amma daga yadda suke zama suyi ta waya da Safiyya da kuma irin kalaman da Safiyya take furta masa ta cikin wayar a matsayin amsar maganganun sa ta fara fahimtar hakan. And then one day she saw a glimpse of him sanda suna video call da Safiyya. Sai da ta dafe kirjinta ta shiga ban daki ta rufe kofa tana mayar da numfashi. He looks exactly like yadda take picturing prince charming dinta. And she fall instantly in love. Har ta sake fitowa basu gama wayar ba, bata jin me yake cewa saboda ear piece ne a kunnen Safiyya din amma daga yadda take ta zabga murmushi tana lumshe ido ya tabbatar wa da Safina cewa kalaman da yake gaya mata are exactly irin kamalan da take so prince charming dinta ya ke gaya mata. Ranar har sai da tayi kuka. Wani irin zafi zuciyar ta take yi mata. How can Safiyya have that? How can she have everything that she wanted for her self? As the good girl that she is, ita ta cancanci everything good ba wai Safiyyan da babu wanda ya isa ya gaya mata magana ta ji ba. Sai dai kuma bata san ta yadda zata bullowa lamarin ba. Ba ta san me zata yi ba. Daga nan ta ajiye duk wasu burikan ta a gefe, dukkan rayuwar ta a gefe ta koma living and breathing for Muhammad. Hanyar duk da zata bi ta same shi ita take so. Har wata rama tayi a cikin kwanaki kadan, har sai da Mommy ta tambaye ta in akwai abinda yake damun ta amma tace babu komai dan tasan Mommy ba zata taba goya mata baya ba wajen cimma burinta. Daga nan soyayyar Muhammad ta fara jan ta, ta fara daukan wayar Safiyya with every chance that she gets dan ta kalli hotunan Muhammad, and the more she looks at him the she fall deeper in love with him. Komai na shi yayi mata exactly irin yadda take so, his smile, ya subhanallah! Bata jin akwai abinda ba zata iya sadaukar wa ba just to have him look at her and give her that smile. Or kiss her with those lips. Or even.…...... Bata jin akwai abinda ko wanda ba zata iya rabuwa da shi ba to get Muhammad. Especially Safiyya. A haka Safiyya ta koma makaranta, taking all the links to Muhammad with her. Wannan semester din hauka ne kawai Safina bata yi ba. Ta yi iyakacin neman da zata yi masa a social media ta rasa shi. Ko mai kama da shi bata gani ba. With him a zuciyarta gani take yi dukkan maza kamar dodanni ne. Bata da wani abu da ta sani game da shi sai sunan sa, Malam Muhammadu, what kind of name is that? Sai dai bata da wanda zatayi shawara da shi idan ba zuciyar ta ba. Zuciyar tata kuma a cike take da soyayyar sa, dan haka zuciyar tata ta bata shawarar da take ganin ita zata kai ta ga samun muradin ta. Wannan yasa Safiyya tana sake dawowa wani hutun ta dauki wayarta la nemo number din sa a ciki. “Pyar💕” la ga any saving, ta gane shine amma ta ga any saving, ta gane shine amma kuma wani irin kishin safiyyan taji tana ji, da kyar ta lallashi zuciyarta ta hana kanta fasa wayar dan takaici. Ta dauki number din kawai tayi saving a tata wayar da "Habibie" Tabbas tana jin labarai iri iri a social media, labarai akan halin maza da yadida basu da amana. Sau nawa saurayi yana soyayya da ya zai fasa ya dawo kan kanwa? Sau nawa saurayi zai hada kawaye biyu yayi soyayya da su a lokaci daya? Sau nawa saurayi zai auri kawa daga baya yazo ya sake auran aminiyarta? Dan Muhammad yana soyayya da Safiyya hakan ba ya nufin cewa ba zai so ta ba ita ma. Musamman tunda dai itana ta a da kyawun ta dai dai gwargwado kuma tafi Safiyya tarbiyya. Har a gurin malamai kuwa taji cewa maza babu abinda suke so irin mace mai biyayya. Basa son mai taurin kai. Safiyya and taurin kai kuwa are five and six, dan haka kwace saurayi a hannun ta ba zaiyi mata wahala ba. Wannan ya kara mata kwarin gwiwa sosai. Ta kuma yi addu'a akan Allah ya bata nasara akan sa, sannan ta zauna ta tsara kalaman da zata gaya masa. Sai da ta gama duk shirin ta sannan ta shiga daki ta rule kofa ta kira shi, Bai dauka ba. Sai da tayi masa five missed calls sannan ta hakura tare da gaya wa kanta cewa yana wani uzuri ne, sai kuma ta yanke hukuncin zata rubuta message ta tura masa, amma kuma tana tsananin, tsananin son jin muryarsa. Ga mamakin ta tun kafin ta tashi daga gurin sai gashi ya kira ta back, sai da zuciyar ta tayi wata bugawa mai karfi ganin sunan Habibi yana yawo akan screen din ta. Ta lumshe ido ta bude tare da sauke ajiyar zuciya sannan ta dauka. Tas taji muryarsa ta fito ta cikin wayar, with his fulani accent, "hello, who is there?" Ta sake sauke wata ajjiyar zuciyar, muryar sounded exactly like yadda tayi tunani, sannan a hankali ta sake tata muryar kasa ta fara gaishe shi, tun kafin ta karasa ya katse ta "I missed calls from this number, wacece? how can I help you?" Tace "wata zuciya ce da ta kasa controlling kanta har sai da ta kira ka dan tayi maka fatan alkhairi tare da shaida maka cewa tana cike da muradin....... ." Ya dakatar da ita "thank you for the call and the care, But I am not interested" and then a sound na katse kira. Ta jima da wayar a kunnen ta ta ma kasa sauke ta kasa, Wani irin daci take ji a ranta, dacin da har sal da ya sauko da hawaye daga idonta zuwa kuncin ta, Shikenan? Just two seconds na muryar sa shine reward din soyayyar ta? Zuciyar ta bata sake breaking ba sai washegari da ta sake gwada kiran sa taji cewa yayi blocking number dinta. Tana shiga dakin Safiyya kuma ta tarar da ita tana ta dariya a waya kuma ta san da shine. "I miss You too. Soon zan dawo ai…..." Safina ta juya da sauri zuwa nata dakin ta fada kan gado ta kama kuka. Kukan da tayi na farko a kansa, not knowing it is just the beginning. To add to her agony, bayan ta kuma samun damar daukan wayar Safiyya da niyyar sake dubawa ko zata samu wata number din sa ko kuma social media handles dinsa, ko dai wani abu da zai yi linking dinta da shi, sai ta tarar safiyyan ta chanja password din watar tata daga wanda ta sani, tayi ta kokarin guessing amma ta kasa bude wayar, daga baya ma sai wayar ta rufe kanta, takaici ya kara rufe Safina ta tashi ta fita. A haka har lokacin komawar Safiyya makaranta yayi, bata samu wani abu da zai sake linking dinta da shi ba. A lokacin ne kuma ta lura da hoton da Safiyya ta chanja na kan screen din ta da shi. Hoton su ne shi da ita a gaban motar ta, motar da aka siya mata saboda gata duk kuwa da cewa a hostel take zaune amma ita aka ki siya mata aka ce ta ringa amfani da motocin gidan. Daga alama Safiyya ce ta dauki hoton ta hanyar selfie, yana sanye da kananan kayan da suka kara fito da kirar jikin sa, ya dan hade ransa kadan hannayensa a cikin aljihun wandonsa yayin da Safiyya take dariyar da take bayyana kyawawan hakoranta, daga alama tsokanar sa take yi. Safina taji wani kishi ya kara sarkafe zuciyarta, ta saka hannu ta toshe fuskar Safiyya ta bar tasa shi kadai tana imagining fuskarta a inda ta safiyyan take. Tabbas ba karamin kyau zasu yi ba. Tabbas ba karamin dacewa zasu yi da juna ba. Sai kuma wani tunani ya zo mata, ta daga wayarta ta bude camera sannan ta saita wayar safiyyan ta dauki screen din wayar a hoto bayan tayi zooming ta tabbatar yayi clear sosai. Ta ajiye wayar safiyyan sannan ta koma kan hoton da ta dauka a wayarta tayi cropping ta cire Safiyya ta bar shi shi kadai. Sai taga ya kara yi mata kyau sosai, ta jima tana kallon sa sonsa yana karuwa a cikin zuciyarta kamar zai fasa kirjinta ya fito. A take zuciyar tata ta sake bata wata shawarar, ta dauka ba tare da musu ba, ta juya zuwa dakinta ta zauna tare da hawa Instagram ta nemo blog din da ta kanga ana posting irin abinda take so, ta tura hoton tare da rubutu kamar haka. "Salam malama, Hide my ID please. Dan Allah ina cigiyar wannan bawan Allahn ne. Allah ya saka min soyayyar sa a cikin zuciyata kuma na rasa a inda zan same shi". Ta tura sannan ta zauna zaman jira. Ranar da wayarta ta wuni ta kuma kwana a hannun ta amma malama bata yi posting ba, washegari ma haka. Daya washegarin ma haka. A ranar ne kuma Safiyya ta sake komawa makaranta. Sai a daren ranar ne ta ga anyi posting request din nata. Nan da nan aka fara comment, masu fada mata bakar magana nayi masu zagin ta nayi, yayin da wasu kuma suka fara yabawa da halittar gwarzon nata suna nuna suma suna so. Babu wata takamaiman amsa dai har bacci ya dauke ta. Da safe tana yin Sallah kan wayarta ta koma ko zata ga wani sabon comment, a lokacin ne kuma ta gani daga wata da ta kira kanta da kanwar sa "laaah, wannan ai Hamma ne. Poster kina ruwa". Babu bata lokaci ta shiga dm din yarinyar da daga baya ta fahimci sunan ta Mufida, la gaya mata ita ce mai cigiyar wannan bawan Allahn, tana so ta taimaka mata ta hada ta dashi. A take Mufida ta gaya mata ba zal yiwu ba, yana da budurwar da yake so sosai kuma bayan ita baya kula kowa. Amma duk da haka bata kyale ta ba, ta ringa yi mata naci. Kira, message, kira, roko Allah da Annabi. Daga baya dai ta bata number din sa tace ta gwada sa'ar ta. Number din dai data dauka a wajen Safiyya ce, amma bata gaya wa Mufida yayi blocking already ba, sai ta sayi wani sim din musamman ta sake kiran sa da shi. Wannan karon ko dauka bai yi ba, ta tura masa message, da aka kwana biyu ta sake kira sai taji shima yayi blocking. Still bata hakura ba, ta koma ta ringa bin followers din Mufida tana nemansa har sai da gano shi. "Muhammad Gidado" ta karan ta sunan shi a fili tana jin sunan ya zauna a dukkan gurbin zuciyar ta, Sai dai account dinsa private ne, ta tura masa friend request, request din da har yau bai amsa ba, Ta yaya? Ta yaya zai so Safiyya ita kuma ya ki ta? Me yasa? A zuciyar ta sai take ganin dan dai kawai bai bata chance bane ba. Shi namiji ne fa ita macece, kuma ba, Shi namiji ne fa ita macece, kuma macen da take da komai da maza suke so a tare da mata. In dai har zata samu chance with him tabbas zata ya mantar da shi Safiyya ta kuma kafa kanta a cikin zuciyarsa. Zata yi amfani da dukkanin baiwar da Allah yayi mata dan ganin ta cimma wanna buri na ta. Kamar amsar addu'ar ta sai ga wannan kaddara ta saukar wa Safiyya, kuma kamar yadda Mommy tace, in dai har aure ya tabbata tsakanin Safiyya da Mustapha to hakan yana nufin rabuwar Safiyya da Gidado, hakan yana nufin high chance for her to get him. In dai har Safiyya tana gidan mijinta kuma ai dole ya hakura ya manta da ita. Sai dai ta cigaba da kiran Mufida da sunan gaisuwa, dan ta kara tuna mata da cewa tana nan fa akan burin ta bata hakura ba. Tana ganin hakan xai kara pushing luck dinta up. Sai dai bata san luck din nata zai yi sama sosai ba, bata taba tsammani ba, kawai ranar nan bayan Mommy da Daddy sun tafi da Safiyya Germany zata haihu sai ga kiran wayar Mufida, wai ana nema wa Muhammad mata kuma tayi wa iyayen su da shi maganar ta har kuma ya amince yace a Kira ta a tambaye ta it she can get married in less than two months. It was like a wildest dream come true, Kamar mafarki wanda bata so kuma bata fatan farkawa daga cikin sa. Abinda bata taba tsammani ba. Ranar rawa tayi tayi a cikin dakin ta ita kadai tana murna. Farko kamar za'a fasa maganar dan da Mufida kawai suke magana amma shi yaki kira, lokacin har raba dare take yi tana addu'a akan Allah ya juyo da hankalinsa gare ta, ta fahimci he was heartbroken akan rabuwar sa Safiyya, duk da dai bata san me safiyyan ta ce masa ba cos she doubt idan zata iya fitowa ta gaya masa cewa ciki tayi in dai har ba cikin sa bane ba. Wannan maganar kuma ita ta daga mata hankali a lokacin, what if cikin jikin Safiyya na Muhammad ne? It is very possible. Amma in ta tuna da dagewar da safiyyan tayi cewa bana Muhammad bane ba sai taji sanyi a ranta, saboda ta san idan nashi ne Safiyya ba zata ki fada ba. Already ta riga tayi plans dinta na yadda auren zai tafi ba tare da Safiyya ta sani ba, ba za ta sani ba har sai an daura vadda babu yadda zata yi, zuwa lokacin uma a yadda taji Mommy tana fada zata iya yiyuwa an daura wa Safiyya nata auren itama, Rana daya kuma sai gashi ya kira din, dadi kamar zai kashe ta, duk da dai abinda ya gaya matan are far from kalaman soyayya amma ya nuna amincewar sa akan auren. Daga nan ta tatattara kayan ta sai Katsina dan gin baban ta, a can take so a daura ta yadda Muhammad ba zai ga komai da zai dangantata da Safiyya ba. A can din kuma ya je ya ganta for the first time, ta yi masa kwalliya ta gani ta fada, kuma yayi mata kyau shima a zahiri fiye da yadda yake yi mata a hoto, amma kuma sai ta fahimci hankalin sa sam baya kanta, sai kuma ta fahimci ya fara kokarin dangantata da Safiyya, wanda a take ta juya maganar ta bagarar da shi. Kamar yadda ta saka rai, yan uwan mahaifin ta sunji dadin kai musu miji da tayi, musamman da suka fahimci cewa akwai maiko a tare da shi. Ita kuwa ba kudin sa take yiwa ba. Shi din take so, kuma zata yi iyakacin kokarin ta taga cewa ta same shi especially yadda abubuwa suka kankama lokaci daya. Taji dadi da Mommy da Mustapha suka baro su Safiyya suka taho wajenta, amma kuma bata ji dadin yadda Mommyn ta dauki auren ba "waye shi? A ina kika samo shiz Shine tat dr da la addabeta da ita, Ita dai Mommy ta san Salina bata da wani tsayayyen saurayin da take kulawa, ballantana ace lokaci daya har auren ta ya tashi da gaggawa haka. "ni bana son gaggawar nan Wallahi, Abi maganar nan a hankali a barsu su fahimci juna muma mu fahimce su" amma ina, yayan baban su har ya karbi kudin aure kuma ya karbi ranar da iyayen Muhammad suka zo da ita. Dole Mommy tayi shiru, sai dai ta tattara ta koma Abuja ta zauna a gidan Hajiya tana cigaba da mita. "Ni hankali na bai kwanta ba. Sam yaron bai yi min ba". Amma a haka akayi. A haka aka daura auren ta da Habibin ta Muhammad. Ranar kowa ya ganta ya san tana cikin tsantsar farin ciki dan sam ta kasa rufe bakin ta tun sanda aka shigo da shi cikin gidan yayan baban su bayan an daura auren ta daga ido ta kalle shi taji kuma an tabbatar mata da cewa shi din nata ne a yanzu, mijinta, halak malak. Tana ji still Mommy tana yiwa ya uwanta mitar yadda angon ko damuwa da ya kebe da amaryar sa bai nuna ba, "ko kallon kirki banga yayi mata ba". Amma ita Safina ko a jikinta, idan bai kalle ta yanzu ba zai kalle ta ne idan sun kebe a cikin gida daya, daki daya kuma akan gado daya Kamar yadda take jl a social media, maza basa taba wuce wannan tayin, basa iya controlling kansu akan wannan abun. Ita kuma tayi niyyar bashi wannan abun har sai ya gode Allah. Wannan niyya ta ta ta saka tun weeks to bikin take ta lodawa cikin ta kayan mata, Ita da kanta ta ringa order daga Instagram vendors tana dirkawa cikinta, ta shafa na shafawa, ta goga na gogawa ta turara na turarawa ta cusa na cusawa. Tayi niyyar Muhammad sai ya mace a kanta, ba Safiyya ba, zata mantar da shi wanzuwar kowacce mace a duniya. Ta shiga online classes da akeyi na sirrin rije miji, a can ta koyo irin shugar da ya kamata take yi masa dan jan hankalin sa, a can ta koyi irin girkin da zata ke yi masa dan jan hankalin sa, magana, tafiya, kwalliya da shi kansa uwa uba bedroom affairs din duk ta haddace komai a kanta. Jira take kawai a kata gidan sa. Rayuwa bata kara yi mata dadi ba sai washegarin daurin auren ta da Mommy ta sanar mata an daura auren Safiyya da Mukhtar. Ji tayi kamar an saka ta a aljanna. Shikenan Safiyya da Muhammad suny rabuwa ta har abada, dan ta tabbatar a irin son da ta san Mukhtar vana vi wa Safivya to auren su mutu ka raba ne takalmin kaza, o da daga baya Safiyya tayi accusing dinta of auren tsohon saurayin ta, zata ce coincidence ne, tunda dai Safiyya bata taba nuna mata shi ba. Koma bata yarda ba matsalar ta ce. Ita dai tunda ta samu Muhammad shikenan. Sai dai tun ranar dinner din su ta tabbatar wa kanta akwai jan aiki a gabanta, ta kata fahimtar girman son da Muhammad yake yiwa Safiyya, amma kuma ai babu yadda ya iya, tunda Safiyya dai matar aure ce a yanzu. Ita bata ma ga dalilin da yasa Mommy ta dauki zafi a lokacin ba, in ma ya tafi ai zai dawo ko? Kawai dai dan Mommy bata son sane tun farko, but she will learn to love him eventually. Da zarar ta shiga gidan sa ta kuma shiga dakinsa komai zai kare. Shi namiji ne ita kuma mace, zata bashi abinda duk duniya babu mai bashi irin sa. Sai dai, tun a ranar da ya dauke ta daga gidan su da kansa ya kaita gidan sa, tun a daren ranar ta fahimci kaddarar da ta kawo ta gidan sa mai wahala ce, ta fahimci ba zata ci wanna jarabawar da sauki ba, Mugun kalion da yayi mata a cikin dakinsa tunda aka haife ta ba'a taba yi mata irin sa ba. Mugayen kalaman da ya gaya mata tun da aka haife ta bata taba tsammanin wani zai gaya mata irin su ba. Jikin na ta da take ji da shi shi yayi wa kalion banza ya kuma wulakanta, sannan ya hankada ta waje ya rufe kofa. Haka taje ta kwanta rungume da pillow a kirjinta, hawaye kwance a idonta, da kyar ta samu tayi bacci saboda bakin ciki da kuma tarin kayan matan da ta dura wa cikin ta. Wata irin soyayya take yi masa zazzafa. Wata irin sha'awar sa take ji mai karfi. A cikin kwanakin da suka biyo bayan nan ta kara tabbatar da gurbin da ya ajiye ta, kamar yadda ya fada mata da bakinsa "you are just a ladder da zanyi amfani da ita to get to Safiyya" ta kuma kara fahimtar cewa duk abinda yake yi mata ko kuma zai yi mata nan gaba saboda safiyyan ne. Shi gani yake yi kamar ita ta raba shi da Safiyya, tuhumarta yake yi kullum bincike ya ringa yi kullum, so yake lallai sai ya san menene ya faru da Safiyya, Ita kuma wannan sai ya kara mata tsanar Safiyya a zuciyar ta, kuma take amfani da dukkanin damar da ta samu wajen gaya wa Safiyya magana a kokarin ta na rage radadin maganganun da shi yake gasa mata kullum saboda tana yi masa wami inn son da ba zata iya mayar masa ba shi. Kullum bakin cikinta shine, ta yaya zai zo Safiyya soyayya mai zafi irin wannan sannan ita kuma ya ki ta? Why? Sai kuma ta sake wani realization din da ya kara sinking zuciyarta, ba shi kadai ba, dangin sa ma basa son ta except for yan gidan su. Ya tabbatar da wannan ne tun ranar da ya kaita gidan kakannin sa da niyyar ta gaishe su. Tun daga kallon da kakar ta sa ta bita da shi ta ji kamar zata rushe da kuka, kallo ne irin na "wannan kuma fa? Daga ina?" Daga baya ma kiri kiri ta ce ta tashi ta bata waje zata yi magana da shi. Kannen mahaifin sa ma da aka tira ta ta gaishe su a sama bata ga komai a tare da su illa rashin acceptance, ita dayar ma da taji suna kira da Ummee ko amsa gaisuwar ta bata yi ba, ko daga ido bata yi bama ballantana ta bata mutuncin kallo, dayar ce ta dan amsa mata ba yabo ba fallasa sannan itama tace mata ta sauka kasa gurin yara. Su kuwa wadanda aka kira da yara tana saukowa wajen su suka daina hirar da suke yi duk suka bata fuska, Daga baya suka fara zamewa daya bayan daya suna komawa cikin wani daki, sai ji tayi sun cigaba da hirar su har da shewa a cikin dakin. Wannan ba karamin kona mata rai yayi ba har sai da ta shiga toilet tayi kuka. Amma a karshe ta share hawayen ta tana jin a ranta cewa ta fahimci dalili6da yasa suka yi mata haka. An gaya musu ita tayi wa Muhammad tallan kanta, kuma ta san wadda ta fada, Mufida ce. Dan haka tun daga nan ta ce a ranta duk ta san inda zata ajiye su har munafukar mufidan, su bari dai kawai ta samu Muhammad a hannun ta. Sai dai kuma a daren ranar Muhammad ya gurza mata wani rashin mutuncin da har yau ta kasa mantawa da shi. Har gorin agolanci yayi mata. Wasa wasa abinda take ganin tafi karfin sa ya juye ya koma cewa ya fi karfin ta. Duk abinda zata yi dan ta kawo Muhammad kan gadon ta tayi amma ya gagara zuwa, duk abinda aka gaya mata yana jan hankalin namiji tayi amma yaki jan nasa hankalin. Ta fahimci ma shi hanyar rabuwa da ita yake nema sai dai yana gudun fushin iyayensa ne. A lokacin ne tana scrolling through Instagram taga post din wata da take neman shawara akan mijinta baya kula ta ta wannan bangaren, ta yi iyakacin iyawarta amma kamar dutse take yi wa, sai ta ji kamar ita ce tayi rubutun, dan haka ta shiga comments dan gain ko zata samu mafita akan tata matsalar, A cikin comments din ne ta ga wata ta bata shawarar da saka masa desire pills a cikin lemo ta bashi, ko baya so sal yayi. DM din matar da tayi comment din ta shiga ta nuna mata kamar ita ce mai post din ta kuma tambaye ta inda zata samu maganin da tayi magana akai, sai matar tace mata tana siyarwa, dan haka babu bata lokaci ta biya kudin har da na delivery aka kawo mata har gida, Sai dai kuma matsalar shine baya ci ko shan abincin ta, ko loma daya bai taba yi ba tunda aka kawo ta, amma duk da haka ta gwada hada masa sobo ta saka a ciki ta kai masa, sai dai kamar yadda tayi tunani yadda ta kai da rana haka ta dauko kayanta da daddare bayan ya bita da bakar magana da mugun kallo. Yana zaune yana juye tea din da ya dafa a cikin kettle din sa zuwa cikin cup. A take ta fahimci ta hanyar da zata bi ta bashi. Da safe da ta dawo gyaran bangaren nasa ta debi pills din guda biyu ta jefa a cikin kettle din da already taji akwai ruwa a ciki. Fatan ta shine ba zai zubar da ruwan ba. Tana leken sa ta taga taga yayi boiling ya zuba ya tati cikin bedroom yana sha. Ta juya ta koma dakin ta, ta kara shanye sauran maganin matan ta tare da tsala wanka ta bade kanta da turare, wannan kukan da ake cewa maza suna yi wa matan su shi take so yau Muhammad yayi mata, wannan tarairayar da take karantawa a novels shi take do ayi mata ita ma yau. She already pictured him crying and begging for her forgiveness tare da alkawarirrika marasa adadi. Sai dai shiru bai zo din ba. Tayi jiran har ta gaji, ga abubuwan da tasha suna damunta sosai tana gujewa kanta fada wa halaka, wannan ya sa ta tashi ta tafi dakin nasa da kanta, ta bude ta shiga har bedroom ta ganshi kwance akan gado ya hadawa kansa ac da fan amma sai gumi ne yaje karyo masa, tasan baccin wahala yake yi, ta san kuma bacci ba mai nauyi bane ba dan haka ta shiga toilet dinsa ta cire kayanta tare da daura towel ta fito ta dan buga gado yadda zai tashi, yana tashin kuwa ta jefar da towel din jikin ta sannan ta durkusa ta dauka tare da yi masa karya sannan ta fita. So take taga karyar taurin kansa. Ai kam ya biyo ta din, kuma yayi abinda take fatan zaiyi din, but it was totally opposite what she expected. Yes, he was more of a man than she ever expected, but there is no affection in his actions. All the kisses, hugs, cuddles and whispering sweet words into her ears that she expected were missing. Bukata ce kawa ta kawo shi, bukatar da ita ta saka masa kuma ita kadai ya biya without even looking at her face, yana gamawa kuma ya ture ta daga jikin sa ya fice daga dakin tare da buga mata kofa da karfi. Ranar tayi kukan da sai da ta dauka hawayen ta zasu kare, gabakidaya hope dinta ya ruguje a tsakiyar kanta. Da wannan makamin ta dauka zata ci shi da yaki amma sai gashi makamin nata yayi backfiring a kanta. Da safe ko kallon hanyar dakin ta bai yi ba ya fita, ita ta tashi ta gyara kanta duk da azabar da take ji a can, sai dai tana fitowa bayan ta danji dadin ruwan zafin da ta shiga sai gashi ya dawo, daga ganinsa sai wani hope ya ratsa zuciyar ta, maybe it wasn't all in vain, ya dawo ne dan ya nuna mata soyayya at last. Sai dai wata azabar ya sake dandana mata, wannan karon bayan buga kofa har da tsarabar takarda ya ajiye mata. Sanda ta gani sai ta dauka kalamai ne irin na nuna yabawa da kuma godiya da alkawarin soyayya har abada, but instead sai ta samu bayanin cewa yayi tafiya kuma ita ma zata iya tafiya gidan su. Ta rintse idonta tana jin hawaye masu zafi suna zubo mata, A ranar, a kuma lokacin ne tayi nadamar auren sa. Dukkan kayan yakin ta sun kare, still nasara tayi mata nisa., Sai dai bata tafi gidan ba kamar yadda ya bukata, ta cigaba da zama, ta fahimci abinda yasa yake so ta tafi shine dan kar iyayensa suce shi ya rabu da ita, so yake ace ita ce ta rabu da shi. Ko da kuwa ba dan haka ba tafiyar zata yi mata matukar wahala a yanzu, dan wannan abin da ya faru a tsakanin su ya kara mata zafin soyayyar sa a zuciyarta yadda har take jin kamar zuciyar tata ba zata iya daukan sa ba, take jin kamar bata da lafiya, kamar zata mutu. Daga haka kuma sai ciwon ya dore, tun tana ganin abin kamar wasa har ya zama gaske, wasa wasa sai gashi likita ya tabbatar mata da ciki ne a jikin ta, cikin Muhammad. Wanna shine greatest news da ta samu a rayuwar ta. Ta san wannan cikin yana nufin kara tamke zaren alakar ta da Muhammad. Zaiyi wahala yanzu iyayensa su barshi ya sake ta. Jin labarin cikin ya sa Mama ta tattaro ta ta dawo da ita gaban ta dan tayi rainon cikin. Taji dadin hakan sosal dan ta fahimci da gaske mahaifiyar Muhammad tana kaunar ta kuma ta san hakan yana da alaka da son da take wa Muhammad din. Anan ta zauna ta jira shi har ya dawo daga tafiyar da yayi bayan wata uku. Sai dai tun a ranar da ya dawo din ta fahimci cewa labarin cikin nata bai yi masa dadi ba, amma ta san duk taurin kan sa in ta haihu dole zai so abinda zata haifa din kuma tana saka ran cewa soyayyar abinda zata haifa zai iya shafar ta watarana. A lokacin ne kuma mugun labarin mutuwar auren Safiyya ya risketa. And her world came crashing on her head. Duk da tasan zaiyi wahala iyayen su da nasa su amine su aura masa Safiyya bayan yana auren ta amma ta san shi ba zai dauke ion sa daga kan safiyyan ba indai ya san bata da aure. Tayi kokarin boye masa maganar amma har gida Mommy tazo ta bashi labari, a take kuma ya bi Safiyyan. Wannan ya sa Mommy ta saka ta a gaba da tambaya akan abinda yake faruwa, sai ta samu kanta da gaya mata cewa Muhammad din ya ga Safiyya tun zuwan da yayi gidan su farkon auren su kuma ya fara sonta duk kuwa da gaya masa da ita Safinan tayi cewa Safiyya tana da aure, ta gaya mata cewa akan Safiyya ne duk matsalolin da suke samu da Muhammad. Ita kuma Mommy ta kwantar mata da hankali da cewa abu ne da ba zai taba yiwuwa ba, babu yadda za'a yi a aura wa Safiyya mijinta. Sai dai a abubuwan da suka biyo bayan nan ta fahimci babu komai a cikin rayuwar nan sai son kai, duk iyaye yayan su suke so. Including iyayen Muhammad wadanda suka shafe idonsu da toka suka ki nunawa Muhammad kuskurensa akan zubewar cikin ta, maman da take kallo a matsayin tana sonta sai ta juya mata baya duk da abinda ya same ta na rashin link guda daya da take ganin zai zaunar da ita a gidan mijinta. A gurin Muhammad kuma ta dauki wani darasi, darasin kuwa shine ba zai taba son ta ba ko da kuwa zata ke yankan naman jikinta ne tana bashi a baki yana ci, kuma ba zai taba daina son Safiyya ba ko da kuwa ita Safiyyan zata ke yankan naman jikin sa tana ci. Ta fahimci cewa her whole life has been a lie. Duk abinda ta dauka akan maza da yadda suke soyayyar su ba haka bane ba. True love truly exists, kuma soyayyar namiji ta fi karfi sosai akan ta mace saboda zuciyar sa tafi ta mace karfi. Idan namiji yana yi miki soyayya ta gaskiya babu wani chanji na rayuwa ko kuma dadewar zamani da zai goge wannan soyayyar. Zai iya aure ma ya hayayyafa amma still zuciyar shi tana ga waccan wadda yake so din kuma ko da ace sun tsufa ne in ya samu dama zai aure ta. Ita ma kuma Muhammad din ya sha gaya mata cewa da ace ba ita bace ba, da ace wata ce daban da bata da hadi da Safiyya da zaiyi zaman aure da ita har ma in Allah ya albarkace su da yaya su hayayyafa. Daga nan sai mission dinta ya chanja daga neman samun soyayyar Muhammad zuwa revenge, revenge on muhammad, revenge for loosing everything to him. Wannan ya sa ta koma gidan sa ta cigaba da zama, tana kara gaya wa kanta cewa in dai tana gidan to ba za'a aura masa Safiyya ba. Daga Daddy har Mommy har su ma nasa iyayen ba zasu yi wannan hadin ba. Ba zasu yarda su hada su kishi ba. Amma hukuncin nata bai yi wa Mommy dadi ba, tayi fushi sosai da ita ta kare mata zagi tas sannan ta kwashe masu taimaka mata ta bar ta ita kadai ga rashin lafiya. Duk da haka bata saduda ba. Ta daura aniyar ba zata bar Safiyya da Muhammad su samu abinda suke so ba, junan su. Mama ta aiko aka dauke ta zuwa gidan ta, hakan yayi mata dadi first dan maran tana da kirki sosai kuma zata kula da ita sosal, amma a yan kwanakin da ta take yi a gidan Maman sal ta fahimci ta chanja mata fuska sosal. Kamar tana kulawa da ita ne dan dole. Sal gabanta ya fadi, zuciyar ta ta raunana sosal. Tsoro ya kama ta, Kar dai Mama ita ma ta daina son ta, kar dai ita ma Safiyya take so yanzu. Wannan ya sa ta gaya mata abinda take tunanin ko da soyayyar safiyyan ta fara kafuwa a ranta zai rushe ta tun kafin ginin yayi nisa. Ranar mama ta shiga dakin da take tayi mata maganar lokaci yayi da ya kamata su koma gidan su ita da Muhammad. Sai kuma ta dora mata da nasiha akan hakuri da kaddarar miscarriage da ta same ta. Sai ta dago kai tana kallon ta tace "Mama" Mama ta juyo tana kallon ta, tace "kun san kuwa abinda ya hada mu rigima a gida ranar da accident din nan ya faru?" Mama ta cigaba da kallon ta bata ce komai ba sai Safina ta cigaba da cewa '"akan kanwa ta ne. Wai kanwata yake so. Yace sai ya aure ta. Ba zaku aura masa ita ba ko?" Mama ta dawo ta rike hannunta tace "ki kwantar da hankalin ki. I already know about it kuma na riga nayi masa magana" Safina ta gyada kan ta "Nagode. Nasan dama ba zaku yarda ba. Kawai ina damuwa ne dan na san halin Safiyya. Ko kun matsa masa akan rabuwa da ita ba lallai ne ita ta rabu da shi ba Zata makale masa Especially not after what happened" cikin curiosity Mama tace "what happened? Menene ya faru?" Safina ta dago kai ta kalle ta sai ta mayar da kanta kasa tace "she is trying to cover up her past" ta danyi shiru sannan ta dago kai ta cigaba "she have a bastard child. Tazo garin nan karatu ta koma gida da ciki. Har yau bata fadi waye uban dan da ta haifa ba. Ina tsoron kar ta makala wa Muhammad". Mama ta zare hannunta daga nata idanunta suna nuna tsantsar tashin hankali. A razane tace "Safina? Me kike fada ne? She is like a sister to you" Safina ta girgiza kanta "she is never my sister. Bata da tarbiyya ko kadan" mama ta mike har lokacin hankalin ta a tashe. "Na shiga uku" ta fada a hankali, ita Safina sai tayi mamakin tashin hankalin Maman ta bude baki sai Mama ta daga mata hannu "I don't want to hear anymore. Wannan issue din sirri ya kamata a tsakanin ku ku family dinta. Bai kamata kina fadawa mutane ba, Ina kuma fatan bayan ni ba zaki gaya wa kowa ba" sai ta juya da sauri ta fita daga dakin, Salina ta bita da kallo cikin mamakin reaction dinta, sai kuma ta daga kafada cikin nuna ko in kula. Sai dai zuwa dare ta fara damuwa da reaction din maman musamman sanda ta aiko a gaya mata ta hada kayanta gobe zata koma gidan ta. Ba kuma ta shigo tayi mata sai da safe ba kamar yadda ta saba. Sai Safina ta samu kanta da yin kuka, ta sake rasa wata soyayyar, ta rasa Mama, Abba dama bata san inda yasa gaba ba. Yanzu Daddy da Mommy ne kadai suka rage mata, sai kuwa Mustapha. Ta koma gidan mijinta still hoping zaman nata a gidan zai hana Safiyya shigowa, still thinking iyayen nasu zasu so ta ko da this ones ne. Amma sai dai sati guda da yin maganar ta da Mama ta na zaune a falon ta ita kadai kamar kullum tana jiran ta ji shigowar motar sa, duk da ba lallai ne in ya shigo ya leko in da take ba. A zaman ne ta dauko wayarta tana chatting da kawayenta, like always, tana ta zuba musu karya akan Habibin ta, bayan sun gama hirar ne kamar an ce mata ta duba status sal ta duba, Pictures ta ga ana ta saka wa kamar kuma duk iri daya ne sai changing position. Yan wwan Muhammad ne suke saka wa, few of them da take da numbers dinsu, suma kuma ta karba ne tun lokacin bikin su a gurin Mutida, tun bayan bikin kuma ba wata magana suke yi ba. Na Mufida ta fara budewa dan gain da tayi kamar Muhammad din ta ne a jiki, gabanta yana muguwar faduwa. Ai kuwa hoton yana gama budewa sai ganin ta tayi ta rikito kasa ba tare da tasan sanda ta fado din ba. Muhammad ne rungume da Safiyya kamar zai tsaga kirjinsa ya saka ta ciki. Fuskarsa dauke da murmushin da bata taba ganin yayi irin sa ba, ita kuma shegiyar safiyyan ta kwantarda kanta a kirjin nasa tare da rufe idonta. A kasa Mufida ta rubuta "alhamdulillah. I can't contain my joy. My Hamma is finally happy" Next kuma dan short video ne na lokacin da safiyyan ta taho ta shige cikin budaddun hannun Muhammad shi kuma ya rufe da ita yana dan bubbuga bayan ta kadan tare da rada mata wata magana a cikin kunne. Shi kuma Mufida tayi captioning da "an daura an daura, Safiyya is finally Hamma's", Then another picture da ya saka zuciyar Satina ta kusan barin kirjinta, still shina a gurin ne, gurin da yanzu Safina ta gane da talon gidan Daddy. Suna tsaye dai still ya unkuyo da fuskarsa ita kuma ta dago tata, fuskokin su dat dana juna, A cikin idanuwansu kana iya hango tsantsar soyayyar junan su. "Shegiya karuwa" Safina ta fada cikin karaji. "Wayyo Allah na" ta karasa tana yar da wayar tare da dora hannayen ta duk biyun a bisa kanta. Ba zata iya kwatanta abinda take ji a zuciyarta ba kamar yadda ba zata iya bada labarin yadda ta fita daga gidan har taje gidan su ba. Burinta kawai ta ganta a gaban Mommyn ta, the only person da take ganin ta rage mata a cikin masu sonta. Tana son Mommyn ta rarrashe ta ta gaya mata karya ne abinda ta gani. "Mommy zuciya ta zata fashe, Mommy zan mutu. Wayyo Allah na. Wayyo Muhammad. Wayyo Abba na". But instead of rarrashi, sai maruka ta samu daga Mommyn na ta, Her🧕🏻 Na jima ina kallon Safina ina kuma sauraron kalaman ta. Abu daya kalaman nata suke tunamin, ranar da aka daura auren ta da Muhammad, halin da na shiga a lokacin da naga hotunan su ita da Muhammad. Furucin da muka yi kusan iri daya ne ni da ita sai dai banbancin Mommy da ta kira ni kuma a kira Daddy. Na sauke ajjiyar zuciya sannan na juya zuwa dakina, a hankali na furta "Karma is a real bitch" Maman Maama✍🏻[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Sixty Three: Sai da na jima a zaune a daki katin Aunty Hajjo ta dawo, na lura duk zuciyar ta a dagule take sanda ta shigo sal kawai ta zauna tana kallo na sannan tace "Allah ya ji kan Safiya" a hankali nace "Ameen" sai ta sake yin shiru sannan tace "ko zaki zo mu tafi gida tare? Maybe you will feel more comfortable there" na girgiza kaina ina murmushi a raina nace, this is my father's house, I am not going anywhere, in na bar gidan mu to gidan miji na na nufa. Ta sake yin ajliyar zuciya "but be careful kinji? Be kind to Sa'adatu. Kar kuma ki kula Safina har kuyi hayaniya kinji? Take very good care of yourself because akwai wadanda suka damu da ke sosai, your father, your husband and junior" ta karasa tana murmushi, nima dan murmushin nayi sai kuma nayi sauri na daina dan kar ta gani, ta sake cewa "da kin yarda zaki bini da kin ganshi ai. Yana nan yana kokarin fara rarrafe" jin dai ba xan kula ta akan maganar sa ba sai ta koma nasihar da take yi min kafin mu fita gurin Safina akan hakkokin miji akan matarsa da kuma hanyoyin da zanbi cikin sauki in sauke wadannan hakkokin har ma da karin kyautatawar da zata kuma kara min martaba a idonsa, Ni kuma a raina ji nake yil can do all that and more to Muhammad. Bata yi min zan cen zama da Safina a matsayin kishiya ba ni ma kuma naji dadin da bata yi min maganar ba cos I wasn't ready for that. Ranar farinciki na ce gwara a barni inyi farin cikin without kishiya talks, kishiyar ma kuma Safina, Daga baya sai Abdul ya kira ya a waya yace tazo su tafi gida, tace min "zan tafi, amma zan dawo gobe muyi maganar gyaran amarya, duk da basan lokacin da zasu saka na tariya ba amma bana jin zai dauki lokaci tunda alhamdulillah akwai masu maganar a dukkan bangarorin " ta karashe tana dariya. Murmushi kadai nayi sannan nayi mata godiya ta kuma raka ta zuwa bakin kofa na dawo ciki dan bana son mu hadu da Abdul ya tsokane ni. Ina komawa daki a fada kan gado na tare da lumshe idona ina jin dadin silence din, in assessing tare da accepting situation dina, Matar aure, matar Muhammad. Na danyi dariya kadan sai kuma hawaye ya biyo bayan dariyar, tun suna fitowa kadan kadan har suka fara fitowa a guje suna wanke duk wan sauran bakin ciki da bacin ran da ke zuciyata dangane da issue din Muhammad, Sal na tashi na kara gyara mayafin jikina sannan na yi sujjada a kasa ina godewa Allah tare da cigaba da zubar da hawaye na akan sallaya ta. Tabbas na dandana rayuwa, na dja wahala irin wadda ko makiyi na bana yi wa fatan ya sha irin ta, amma Allah ya kasance a tare da ni every step of the way, shi ya rike hannuna yayi guiding dina tare da haska min hanyar da nabi, shi ya kasance tare da ji a lokacin da nake tunanin na rasa komai, shi ya taya ni zabin abinda yake shine alkhairi a gare ni sannan kuma ya juya lamari na in the most simplest way possible. A cikin ikon sa da rahamar sa yanzu kusan duk abinda na rasa sun dawo gare ni, abubuwan kuma da ba zasu dawo ba sai ya saka min hakuri da dangana a zuciyata tare da fatan hakurin zai zama kaffara a gare ni. Na dago zaune daga sujjada ta ina goge sauran hawaye na, ni na san wannan ba shine fadan karshe a rayuwa ta ba, ni na san wannan Mabudi ne kawai na wata sabuwar chapter a rayuwa ta, ni na san jarabawa ta bata kare ba for as long as I am alive, amma kuma bana jin tsoro ko kadan dan na tabbatar as long as zan kasance tare da Allah shima zai kasance tare da ni, zai kuma yi riko da hannayena ya taya ni fighting battles dina, battles din na tabbatar zany wining tunda ina tare da Allah na. Daga nan kuma sai na tashi na gabatar da sallar ishain da ban yi ba. Ina cikin sallar Esther ta shigo ta ajiye min abinci ta zauna tana jira na har sai da na idar sannan na juyo ina kallon ta. Fuskar ta kamar anyi mata albishir da Jesus dinta ya zo "Madam! Congratulations. Ina cikin murna sosai. Mijinki mai kyau mai kyau mai kyau. I cannot tell you how happy I am for you" nayi murmushi "thank you Esther. And I don't know how to say this to you but just know that kinyi matukar kokari gurin tabbatuwar wannan maganar" ta dan bata rai tana tunanin kokarin da tayi sai kuma ta sake washe baki "the pepper soups! Guda uku nayi. Da na naman rago, dana kaji da kuma na kifi"., Nayi murmushi kawai bance komai ba sai ta sake cewa "dazu na ban san angwayen zasu zo ba banyi musu komai ba, sai ga Alhaji Ahmed nan ya kawo snacks da yawa yace in kai musu da drinks" na gyada kai kawai "ya kyauta. Ya kyauta sosai'",. Ta nuna min tray din da ta shigo dashi "white rice na dafa miki da sauran fish pepper soup din dazu Na san kina so. And I made your timoothie!" Ta fada with excitement. Na dauki cup din a zuka through straw din da yake saman sa yayin da ita kuma ta zuba min ido tana kallona har na ajiye sannan nace "duk kamun kafar ki dai ba zan tafi da ke ba. Kina nan gidan" ta bata rai "haba madam haba madam" nayi dariya "sai abinda Mommy tace, kin san dai ba zan dauke mata ke ba ko?" Ta gyara zama "shawara Madam, na yarda a kawo wasu masu aikin, and then in kin tashi tafiya I will just say tunda akwai wasu ni zan biki, kinga ba zata ce komai ba" nayi shiru bance komai ba sai ta sake cewa "please!'" Nayi ajjiyar zuciya "okay. Shikenan. Get them. Guda uku, Sai mu gwada su mu gani" ta mike da sauri tana murna "na gode, thank you Madam". Tana fita na bude abincina na ga yadda ta kawata white rice din with vegetables. Pepper soup din ma daga gani ba wai saura bane ba sabo ne tayi min, duk kuma na san na kamun kafa ne. Sai na samu kaina da cin abinci na cikin nishadi, abubuwa da yawa suna yawo a kaina, plans nake making iri iri, in saka in warware in girgiza kai a inyi murmushi duk ni kadai. Sai a lokacin na tuno da cewa tun rana waya ta a kashe take, Allah kadal ya san sau nawa Muhammad ya kira ni a yau din nan, To dama ya lafiyar kura? Na dauko wayar bayan na gama cin abincin na kira Esther tazo ta kwashe kayan. Na kunna, messages suka shigo min sosai, na sa na fara nema kuma shi na fara budewa na karanta. "I am yours, and you are mine. Forever and ever" Nayi murmushi na sake karantawa sannan na kara karantawa. "Ina sonka sosai Muhammad" na fada a hankali. At a point na fitar da rai completely da auren Muhammad. A lokacin da na zabi Mukhtar da kaina na dauka na rabu da Muhammad har abada. Na dauka kuma zan zauna da Mukhtar har abada. Amma ashe Allah yana nasa plans din. Naji ina son kiranshi inji muryarshi, for the first time as his wife, dan na san shi yayi ta kira na wayar a rufe, amma sai na samu kaina da kasa yin hakan. So nake ya fara kirana, ajin nan dai ba zan sake shi ba sai na ja abina. Sai dai shiru bai kira ba. Har na tashi na dan motsa jikina saboda abincin da naci yayi min nauyi na kuma gyara gurin kwanciyata tare da rage kayan jikina nayi shirin bacci amma bai kira ba. Sal na kwanta akan gado a fara karanta sakonnin da aka turo min. Sal na lura da yawa yan uwan mu na Kano sun samu labarin daurin aure na ashe, duk sun turo min sakon taya murna, Salima da Salim ma sun turo min, salima ta ce ta kira wayar a kashe amma zata zo gobe. Sai kuma wani message from unknown number '"Ina miki son da ba zan taba iya hakura da ke ba Safiyya, ina miki son da zan iya taba bari wani ya same ki ba bayan ni Safiyya. Especially not him" Na mike zaune tare da sake karanta message din. Tabbas na gane wanda ya turo sakon duk da ba number dinsa bace ba kuma bai rubuta sunan sa ba. A take nayi wa security na forwarding message din tare da number din. Minti biyu suka yi responding. "An sauke layin. But we will be at alert. Be careful". Har na ajiye wayar sai kuma na dauka da kira chief of the security din nace masa "in kun ganshi anywhere around this house or around me, ku harbe shi a kafa ku mika wa police shi. You still have the restriction order?" Yace "yes boss, just lock your doors and windows. We will get you a gun tomorrow" Na katse kiran tare da dafe kaina ina jin raina yana matukar baci. It hurts me a lot idan na tuna da Mukhtar din da na sani, Mukhtar din da na tashi together with, sannan kuma na tuno wannan ranar, na tuno abinda yayi min wannan ranar, Bana jin da ace wani ne daban abin zaiyi min ciwo irin haka, ko da kuwa ace Mustapha ne. Sai da na tuno da Mustapha sannan na tuna da cewa naga sunansa as I was scrolling through messages, amma ban dauki wayar ba sai na tashi na rufe kofa ta na kuma tabbatar dukkan tagogin dakin da kuma na toilet a rufe suke. Na kuma tabbatar wuka ta tana nan a inda nake ajiye ta sannan na koma na kwanta. Mukhtar ba zai kuma taba ni ba, har abada. Message din Mustapha na nemo, "Naji abinda kika yi. Kin kyauta" Ban bashi amsa ba kawai na fita ina jin nadamar budewa, suna so su bata min daren farin ciki na. Gashi Muhammad din ma yaki kirana. Amma sai naki bawa kaina damar yin bacin rai, not tonight. Instead, sal na dauko chats din mu da Muhammad nayi ta karantawa ina murmushi tare da dariya at the same time, a haka har bacci ya dauke ni, Cikin baccin naji wayata tana kara, na bude idona da kyar sannan na lalubota, sai lokacin ma na fahimci ko fitilar dakin ban kashe ba bacci ya dauke ni. Sunan Muhammad na gani, na duba time naga 12:45, na dauka na dora akan kunne na amma bance komai ba sai yace "kar dai kice min bacci kike yi" na juya idona kamar yana kallo na sannan cikin muryar bacci nace "to me zanyi idan banyi bacci ba? Tunda babu wanda ya damu da ni ballantana ya kira ni yay min hira" ya. danyi dariya "amma kin bani mamaki. Ni da na dauka yau kwana zaki yi kina rawa da murnar farinciki burinki ya cika?" Na san tsokana yake ji da ita nima cikin tsokanar nace "ashe abinda kake yi kenan shi yasa baka kira ba? Kana can kana rawa da murnar burin ka ya cika. Na san fa yadda ka mace a kaina baka ji baka gani" yace "ohh da gaske. In na mutu a soyayyar ki ma ai tare muka mutu ni da ke. Har da kuka fa dazu saboda murna. Murnar kin samu santalelen bafulatani kama ta" nayi dariya ina jin baccin yana barin ido na nace "shi yasa naga ai har nayi baccina amma kai ka kasa bacci sai da ka kira kaji murya ta. Dan in baka ji ba ba zaka iya bacci ba" yace "wannan kuma kin fadi gaskiya. Ba zan iya barci ba sai naji muryar ki. Sai yanzu na shigo gida tun dazu ban samu privacy ba. Ina ta fama da baki. Bayan bakin kuma sun tafi sai muka zauna da Abba da Mama muna ta magana. I told them all about you. But sai na fahimci sun san some parts of the story" na lumshe idona na bude ina jin girmansu yana karuwa a zuciya ta for accepting me the way I am kuma ba tare da wani bata lokaci ko wasu conditions ba. Ya cigaba "Abba was a bit concerned about all the ...….. He was concerned about the..........." Na karasa masa "about the wealth" yace "yeah, right. But then daga baya sai Mama ta fahimtar da shi. Naga alama kin samu fada sosai a gurin Mama" ya karasa da farinciki a muryar sa, nace "nima fadarta mai girma ce a wajena" yayi ajjiyar zuciya "ni yanzu damuwata itace naga alamar suna son su la lokaci kafin ki tare wallahi. Abba wants to renovate the house, wai zai mayar da Shi up to your standard" na danyi dariya "menene standard din nawa? I thought it was built to my taste da mako?" Yace "yes, but yanzu suna ganin wai gidan yayi kadan, ni banga kadan dinsa ba. Nayi magana kuma Mama ta harare ni tace min marar kunya" nayi dariya "inye, rich kid. Kana zaune ana yi maka komai ko?" Yace "not anymore. Abba said this will be the last. Dama sunce in suka yi min aure sun daina yi min komai. Amma auren ne har yanzu ba'a gama ba" ya karasa yana dariya. Nace "uhmm, dan gata" yace "ba zaki bari ba ko? Please ni dai in sunzo sunce lokaci mai yawa zasu saka ki ce ke next weekend kike so" nayi dariya "kar ka damu. Ni gobe ma zan taho. Kawai ka samu daki daya a gidan ka share mana shikenan". Haka muka ta hira, lokaci yana ta tafiya bamu sani ba kuma munkan mu ba zamu ce ga abinda muka tattauna a hirar ba. Sai jin sanyin gari nayi yana ratsa ni sannan na kalli agogo, nayi sauri na bude ido. "shikenan zaka saka gobe in tashi da kumburarrun idanu. Go and sleep Mr Man" yace "duk wanda yace miki me yasa baki yi bacci da daddare ba ki ce masa nine na hana ki yin baccin, in kika ce haka zasu kawo ki da wuri" nayi murmushi kawai "good night" yace "sai dai good morning kuma yanzu ai. But just one more thing please, Tambaya ce da n'" nace "Allah yasa na sani" yace "Akwai abinda ya damyi confusion dina, lissafina bai tafi dai dai ba gaskiya, dazu ma muna maganar da Mama sai naga kamar ta share maganar bata son y" na danyi shiru ina jin sa ina tunanin wanne lissafi ne, sai yace "date din da kika gaya min uncle Ahmad ya kawo sakon takardar nan. Har zuwa yanzu a lissafina ba'a yi wata biyu ba ma ballantana uku. I thought sai kinyi wata uku tukunna or somewhere close to that. I know you and Daddy all have the Islamic knowledge concerning that so dole akwai explanation" yayi shiru nima nayi, na gane abinda yake nufi na kuma yi realizing yadda yake avoiding mentioning sunan Mukhtar. Jin nayi shiru sai ya sake cewa "kin gane abinda nake nufi? I just want to know why" direct na bashi amsa "saboda banyi masa idda ba. Babu iddar sa a kaina" ya danyi shiru kamar bai ji me nace ba amma na san yaji, sanda yayi magana naji relief mai yawa a tare da muryar sa "and hakan yana nufin me kenan?" Nace "ni ma ban sani ba. Sai dai a tambayo" yace "wa za'a tambaya? Bayan gaki nan ina tambayar ki Kawai ki fada min abinda hakan yake nufi n ban sani ba" nace "to ni ma ban sani ba, Good night" yace "zaki fada ne, Zaki yi min dogon bayani ne in details…..." Na katse shi "good night" sai na katse kiran na ajiye wayar ina murmushi duk kuwa da cewa kaina yayi min nauyi sosai saboda baccin da yake cikin sa. Sai bayan da nayi sallar asuba sannan nayi bacci mai nauyi, ban tashi ba sai around 12 shima kuma dan ina son inje inga Daddy ne tunda jiya ma ban samu ganin shi da daddare ba. Da sauri nayi wanka na shirya cikin doguwar rigar atampa na fito as usual banyi kwalliya ba, ina fitowa Esther ta shiga ta fara hidimar gyaran dakin dama jiya duk na hargitsa closet din. Dakin Daddy na wuce direct, na tarar da shi tare da uncle Ahmad suna magana, ina shiga suka juyo suna kallona suna murmushi "amarya" uncle Ahmad ya fada, nayi kamar zan koma da baya dan kunya, sai Daddy ya miko min hannunsa "come here" na karasa na saka hannuna cikin nashi sannan na zauna a kusa dashi tare da gaishe shi, ya amsa na gaishe da uncle Ahmad shima ya amsa tare da cewa "ya shirye shire?" Sai nayi kamar banji ba sai yace "umman ku zata shigo in anjima ai, Salima zata zo itama kuyi magana. Duk abinda kuke bukata sai kuyi magana kinji? Ko ba zaki fada min ba ki fada wa Salima sal ta gaya min" a gyada kai idona a kasa, Daddy ya dan matsa hannuna a cikin nasa na dago ido na kalle shi sai yace "kin shiga gurin Sa'adatu?" Na girgiza kai "yanxu na tashi, na fara zuwa wajen ka ne amma yanzu zanje wajenta" ya gyada kai "alright ki shiga. And be nice to her" nace "to" har zan tashi kuma sai na sake cewa "Daddy kunyi magana da Hajiya? Ta sani?" Yace "eh, I told her tun kafin a daura. And I will call her yanzu in gaya mata an daura din, jiya na manta ne" uncle Ahmad yace "kar ka dora wa kanka laifi yaya, ai ba kai ya kamata ka gaya mata ba, Sa'adatu ce zata gaya mata" ni dai sai ya zame hannu na na tashi, ina jin Daddy kamar kar ya saki hannun nawa, sai naji zuciya ta wani iri, he is already missing me. Har na kai bakin kofa kuma sai uncle Ahmad ya sake kira na, na juyo sai ya nuna min gurin zama dan haka na dawo na zauna sai yace "na manta ba muyi maganar ba. Akwai kayanki na gidan Mukhtar, naje na gansu an hada komai a waje daya, na saka yau za'a kwaso su a kawo su nan gidan, ban sani ba ko akwai abinda zaki yi amfani da shi a ciki. Kayan sakawar ki da kika bari a can ma na saka Salima ta hado miki su, tare da lefen ki ashe duk baki yi amfani da komai ba, in anjima in zasu zo zasu taho miki da su", Na danyi ajiyar zuciya sai kjma naga kamar ni duke jira suji abinda zance, Daddy zainiya fadar abinda za'a yi ko ya gaya min abinda zanyi amma Daddy baya min haka, baya taba yanke min hukunci sai dai ya tambaye ni abinda nake tunani in na fadi abinda ya san ba dai dai bane ba sai ya gyara min zuwa abinda yake dai dai ta hanyar bani shawara. "Ni sam ban saka lissafi da su ba. Banyi tunanin komai a kansu ba. Abubuwa da yawa ba'a taba using ba except for kujeru da aka dan zauna akai. I don't know ko za'a ajiye wa Salima tunda babu abinda zasuyi har Allah ya kaimu bikinta. In ma kuma bata son colours din ko design din za'a iya siyarwa a siya mata wasu" Uncle Ahmad ya fara girgiza kai, "kayan masu tsada ne sosai, abubuwa da yawa ba sai an sake siya miki ba. Kayan suna da yawa sosai" ya yi ta fada irin ka rasa abin cewa din nan. Ni kaina na san kayan masu tsada ne dan sanda Mommy tayi order din su sai da na jinjina kudin amma tace su suka fi dacewa da ni. But there is trauma attached to them and I cannot use them. Kuma wanna kyautar ina ganin zata kara bonding zumuncin da ya fara samun baraka tsakanin mu. Daddy yana murmushi yace "kai da ba kai aka bawa ba ina ruwanka? Kanwarta ta bawa ai" jin hakan sai nasan yayi accepting decision din nawa, na sake mikewa sai uncle Ahmad ya sake cewa "at least ki karbi kayan lefen to. Ni na siya dama ai ba shi ya siya ba, sai ki kara akan dinkunan da zaki yi na zuwa can gidan" na gyada kaina nace "zan karba, Thank you Uncle" na fada dan bana son inyi jayayya da shi kar ya dauka wani abun ne daban. Dakin Mommy na wuce duk kuwa da yadda Esther take bina da cup din coffee a hannun ta, bata falon ta, babu kowa a falon dan haka na wuce bedroom din ta ina fatan kar mu hadu da Safina a can. Nayi knocking na tura kofa tare da sallama ina jin yadda gaba na yaje faduwa, ina cherishing relationship dina da Mommy sosai ina kuma kokarin avoiding abinda zai lalata shi. Tana kwance akan gadon ta amma idonta biyu, ta dan juyo ta kalle ni sannan ta mayar da kanta ta kwantar, na zagaya ta side din da fuskarta take na zauna akan carpet nace "good morning mommy" ta bini da kallo tare da dan motsa bakinta kadan ba tare da naji abinda tace min ba, Banji dadin yanayin fuskar ta ba dan idanunta sun nuna bayan kukan da tayi jiya bata yi cikakken bacci ba. Na cigaba da zama a gabanta amma bata ce min komai ba har wajen mintuna goma, ina so muyi magana dan haka nace "I am sorry Mommy" a hankali tace "for what? What are you sorry for?" Na danyi shiru ina tunani, menene abinda nayi wa Mommy ne? Sai kawai nace "I am sorry for whatever I did that made you cry" ta dafa gadon ta mike zaune tare da jingina bayan ta da headboard. Tana kallona tace "tell me something Safiyya. Tunda Allah ya hada ni da ke akwai abinda na taba yi miki that made you feel I am not your mother?" Na danyi tunani kadan, I can mention a few things but I didn't, sai na girgiza kaina "babu" ta cigaba "but you still think I am not good enough to be your mother ko? Ke ma irin ta mahaifin ki ne ko? Kullum kina tunanin zan cutar da ke ne ko? Kina kallona a matsayin kishiyar uwa, bayan kuma da ace Safiya tana da rai da ba zan taba zuwa gidan nan ba" na girgiza kai "ko tana da rai Mommy dole zaki zo ai. Twins kuma fa?" Tayi shiru tana kallona "you are always smart, with your words with your actions and with your choices. You have no idea how much hard it was to raise you, especially with idanun babanki da ko kallon banza aka yi miki sai ya chanja fuska, especially with idanun mutane akai suga me zanyi, Wannan ba yar ta bace ba wadancan ne yayanta. Kuma bana taba yin dal dai. Adam will criticize, Ahmad will criticize, Hajiya will always have something to say. But I did my best, Through it all I did my best. Idan ku baku gani ba Allah ya gani ai. Ban taba cutar da ke ba kuma ba zan fara daga yau ba. Yes naso Mustapha ya aure ki amma ban tura shi yaje ya ci zarafin ki ba. 12 1d AM Tabbas ina son Safina amma ba zan goyi bayan ta rabaki da saurayin ki ta aure shi ba. Ni bana son yaron ma. Har yanzu ma da kike matsayin matarsa still bana son sa. Ban sani ba ko nan gaba zaiyi abinda zai saka in so shi. Amma ina so daga ke har Adam ku sani cewa it hurts so much that you do not trust me after all these years, that you treat me like an outsider ba wai uwa ba da ya kamata ace ta fi kowa kusanci da ku, ba zaku bude baku ku gaya min magana kuyi min bayani ba." Ta karasa hawaye yana bin fuskarta. Naji zuciya ta ta kara karyewa, na tashi na zauna a bakin gadon nace "kiyi hakuri Mommy, dan Allah ki daina kuka. I am sorry, I never meant to hurt you wallahi ban so na saka ki kuka. Ke kadai ce uwata, ke kadai na sani uwata kuma ke zaki cigaba da zama uwata. Dan Allah ki yale min" ta girgiza kanta "there is nothing to forgive ai. Kawai yana yin tunanin ki akaina nake so ki gyara. In ma da akwai na yafe miki. Allah ya ji kan Safiya" nace "Amen. Nagode Mommy" sai kuma na zagaye ta da hannayena na rungume ta ina jin wani iri a raina. Nayi missing our hugs and kisses. Nayi missing yadda muke zama muyi hira muyi wasa da dariya. Nayi missing dinta. Ta zagaye ni da hannayenta ita ma sannan ta dan buga bayana kadan sai kuma ta sake ni. Na tashi na fita daga dakin ina jin nauyin zuciyata ya dan ragu akan issue din. Ina gama breakfast a kasa su Umma suna zuwa tare da Salima da uban lodin kayana, kayan sakawa ta da kuma akwatinan lefe na da har yau Allah bai bani ikon bude su na ga menene a ciki ba. Aka shigar da su wani daki a ka ajiye su. Sai a lokacin Mommy ta sauko still kana ganin ta ka san tana cikin damuwa. Suka gaisa sama sama da Umma, a raina ina ta addu'ar kar Umma ta ce zata gaya mata magana kuma sai naga bata yi din ba. Daga nan Umma tace uncle Ahmad yace suyi maganar shire shiryen tariya ta, amma already Daddy yace baya son biki, baya son duk wani abu da zai jawo attention din mutane, nima dama banyi lissatin yin biki ba, Ina dai tunanin shirya walima for my friends da sukayi ta mitar na watsar da su tun lokacin wancan bikin, Nan na gaya musu cewa ni walima kawai dan shirya for my friends, Umma tace to suna nasu Mutanen sai su zo walimar kawai, a take Salima tace ba zai yiwu a kawo mana tsofaffi cikin walimar mu ba, suna ta musun su sai ga Aunty Hajjo nan tazo itama. Na gaishe ta nan take ta shige cikin maganar itama, ita ta goya wa Salima baya. "A'a ba zaku shiga walimar su ba. Kinga Salima, ku chanja wa event din naku suna daga walima zuwa wani sunan da zai nuna na yammata ne kawai, in ba haka ba har da kakanni sai kun ganj" Ni dai ban ce musu komai ba. Mommy ma few words kawai take dan sakawa dan hankalin ta gabaki daya kamar baya gurin kawai a zaune take. And I asked myself again ina Safina take? Ko dai ta koma gidan Muhammad ne? Ban samu amsar ba sai da na tafi daki yin sallar na hadu da Esther sai na tambaye ta ko taga Safina a gidan? Sai tace "ya da dare bayan kin taho daki Mustapha yazo ya dauke ta. Na gyada kai, maybe gidan Hajiya ta tafi ita ma, Ina yin sallar maimakon in koma kasa sal na dauki waya la na kira Muhammad muka sha hira, ya gaya min wai already har sunje da Abba kamfanin da zasu vi musu Renovating gidan, har sun zabi plan, "kamfanin su Ya Amen ne fa, they are into construction, Dama su suka gina gidan tun farko, yanzu ma kuma su zasu yi aiki a kansa" da ya fara tsara min yadda suke so ayi wa gidan sai da naji kana yana neman bugawa "ni fa ba gane wa nake yi ba wallahi. Ka barshi kawai in an gama naje sai in gani" ya dan mararaice "inzo in dauke ki yanzu muje in nuna miki?" na danyi dariya "me zaka nuna min tunda ba'a fara komai ba?" Ya danyi shiru "yeah, right. To wani abu zan nuna miki daban. Wani abu ne da nasan kina son gani" nace "dauki hoton sa a waya ka turo min" yace "it is too big, ba zai dauku a waya ba. Please inzo muje?" Nace "ko kazo ma ba zan fito ba. Wallahi gidan mu a cike yake da iyaye na. Ba zan wuce su in tafi gurin a ba" yace "ni fa mijin ki ne. Maganar wa zaki ji? Tawa ko tasu?" Yadda ya fadi maganar da authority ya sa na mararaice "Please Baby, dan ni suka zo gidan fa, Kuma kawai sai in bika mu fice mu bar gidan?" Ina maganar Salima ta bude kofa ta shigo tace min "Fiyya ki zo ga Hajiya nan tazo" nayi mata alamar ina zuwa sannan nace masa "kaji ko?" Ya danyi shiru sannan yace "Hajiya Maryama?" Nace "yes ita" yayi ajiyar zuciya "hey Piya! How are you coping? I mean ya kuke ciki da Mommy and her children?" Na sauke ajjiyar zuciya ina jin dadin concern dinsa nace "yanzu dai zanje gurin Hajiya. We will talk about it later insha Allah" yace "okay. Just take care of yourself kinji? Kar ki bar komai ya bata min ranki. And ....... Zan shigo in an jima da dare idan sun tafi. Kuma babu zama a falo with the cctv thingy" nayi dariya "okay. Bye Baby. Love you " Da sauri na sauka kasa, ban san yadda Hajiya zata dauki maganar ba kuma tana daga cikin mutane masu muhimmanci a rayuwa ta wadanda no matter the situation ba zan so mu samu sabani ba. Tana zaune a kan carpet ta mike kafarta, na sauko reluctantly ina tunanin abinda zata ce min sai cewa tayi "ina akwatin kayan ki? Nace wa adamu fa ya gaya miki ki hada kayan ki tare zamu tafi, wannan karon ni zanyi gyaran amarya" Aunty Hajjo tayi saurin cewa "a'a fa. Wannan aikin ai na iyayen amarya ne ba kakanni ba. Ke dai zaki iya kawo gudummawar abinda kika tara" na dan saki raina kadan tare da karaso wa nace "Adam, Hajiya, ba Adamu ba" ta jeho min throw pillown da yake kusa da ita "jaira, Adamu zan ce ba zance Adam din ba" nace "already ai kin fada". Aka sake yin dariya, Daga nan suka cigaba da lissafe lissaten su yayin da ni kuma muka ware da Salima muke namu. Decisions din mu na kayan da zan saka ne a event guda daya da nace zanyi sai kuma na kai amarya. Amma kuma dai bamu sani ba ko gidan su Muhammad zasu shirya wani abu. Karshe dai muka ce zanyi dinkuna na fitar biki set biyar in case, sai kuma sauran dinkunan da zanyi. A take na dauko system dina muka fara neman material, shiga can fita can da kyar muka samu guda biyu da suka yi mana, to matsalar kowanne sai an nemi abun da za'a hada shi da shi. A karshe dai kawai muka yanke shawarar neman fashion designer da zata yi mana komai. A karshe dai Salima kin bin Umma tayi tace a waje na zata zauna "akwai abubuwa da yawa da zamuyi kuma bamu da lokaci" Umma tace "au har kun saka ranar ne mu bamu sani ba?" Sai akayi dariya kawal. Da daddare Muhammad yazo kamar yadda yace, na san da zuwan na sa dama dan haka naje nayi wanka na shirya cikin riga da skirt na atampa na gyara gashina nayi daurin dankwali mai kyau. Dinkin ya zsuna das a jikina, na shafa turaruka na masu dadin kamshi, Salima tana ta tsokana ta wai sai ta raka ni ta gaya masa ita ta shirya ni ko zai dan miko mata wani abu. Ban samu lokacin yi masa girki ba amma na saka Esther tayi masa kuma na san zata fitar da ni kunya. Amma mutumin nan yana zuwa sai yayi zaman sa a mota sannan ya kira ni "ina waje a mota" nace "waje kuma? Ka shigo mana ga ...." "Not a chance. Ki same ni a mota" ya katse kiran. Na sauke wayar daga kunnena ina hararar ta. "Kinji wai ba zai shigo ba" na gayawa Salima da take bina da kallo, tace "to me yasa? Ciki ba yafi sirri ba?" Na dan yi murmushi kawai dan nasan rashin sirrin cikin gidan shi yasa ya zabi zama a waje. Na dauki mayafi na na yafa ina jin wani iri, wasa wasa kuma sai zuciyata ta fara bugawa da karfi. Wata zuciyar tana gaya min in cire kayan inyi zamana a daki in kashe wayata. Amma banyi hakan ba dan nima ina son ganin sa amma ina tsoron ganin na sa. Muhammad yanzu miji na ne, kuma ban yarda da wannan neman privacy din na sa ba, Haka dai na taka na fita, a raina ina tunanin wanna shine zuwan Muhammad gurina gidan mu da niyyar zance na farko in all the years da muke tare, na bude karamar kolar gate na fita waje ina neman motarsa. A inda ya saba parking a tsallaken mu na duba ban gan shi ba, sai daga baya naga motar tashi a jikin gidan mu cikin inuwar katangar gidan, Na sake jin bugun zuciya ta ya karu. Na dan tsaya daga bakin gate din na dauko waya ta na kira wayarsa, ina jin ta tana ringing a cikin motar amma bai daga ba. Na karasa kusa da motar na tsaya zuciya ta tana kara gaya min in koma cikin gida, sai naga an bude kofar bayan motar, na dan tsorata kadan duk da ina kallon security na a bakin gate sai naji muryar sa yace "matsoraciya, come in" na kalli motar, Muhammad bashi da gaskiya, bayan kin shiga cikin gida da kuma yin packing a cikin duhu shine ya koma seat din baya ya zauna nima kuma yake so in shigo bayan. Na makale kafada "ni dai ka fito nan" ya kunna fitilar cikin motar "kin ga fa, kaza na kawo miki" ya karashe maganar yana nuna min ledojin da suke gabansa. Sai kuma ya bini da kallo ta hasken cikin motar da ya haska ni "wow. You look good" na dan tabe baki "ni dai ka fito" ya danyi dariya "kar dai ki ce min ke matsoraciya ce har haka. I just want us to talk in private, shikenan kawai" Na bishi da kallo, yayi kyau sosai, kamar ma sabon aski da gyaran fuska yayi, kamshin turaren sa da kamshin motar sa suka kara kawata min shi. "magana kadai zamuyi'" na fada ina hade rai. Yace "yes, haka nace. In ba magana ba me kike tunanin zamuyi?" Ya fada yana kankance idonsa, na dauke kana nace "kayi alkawari?" Ya daga gira "nayi alkawar'" nace "ka rantse" yayi dariya tare da dafe kansa "Please Piya, ki shigo mana. Bana son mutanen waje suna gane min ke saboda kyan da kika yi. Eh nayi alkawari I will not do what you think I am here to do" ya karasa da dariya a muryarsa sannan ya matsa tare da bani space din shiga. Sai da na sauke ajjiyar zuciya tare da karanto addu'ar da ban san ko ta menene ba sannan na shiga na zauna a dofane daga bakin kofa. Ya bin da kallo sannan ya girgiza kai kawai, sai kuma ya zuro hannunsa ta saman cinyata ya jawo kofar ya rufe sannan ya kashe fitilar da ya kunna, Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Sixty Four : Fearful A wannan lokaci da muke ciki na sanvi kina bugatar abubuwa da zaki ci/ sha Wanda zai saukar miki da wadatacciyar niima Kuma ya Kara miki dandano da kuzari. Akwai abubuwa da dama da muke amfani da su a cikin gida Wanda in kika ¡ya sarrafa su zasu magance miki matsala ta oza room musamman ma daukewar niima da sauransu. To 'yar kuwa me kike Jira? Kiyi kokari ki shiga wannan aji da zamu gudanar inda zaki koyi abubuwa kamar maganin sanyi, maganin Karin niima, maganin Kara dandano da sauransu a saukake ba tare da kin sha wahala ba akan kudi qalilan. Ga masu bugatar shiga wannan aji zasu iya Yi mun magana WhatsApp direct.wa.me/8033308307 ko Kuma kuyi joining wait-list group dinmu domin Karin bayani. https://chat.whatsapp.com/ L1PcrHctun5JIQnBHmOlih Duhun da na ga ya mamaye idona ne ya razana ni lokaci daya, yana tuna min da wancan duhun. Na fara kokarin bude kofa sai ya rike hannuna "Hey! What's wrong" ya fada with that deep voice of his da nake finding soothing a baya amma a yanzu sai na jishi kamar as a reminder to him being a man. "Please ka kunna fitila, I have phobia for darkness" na fada murya ta tana rawa hawaye already ya fara taruwa a idona. "Okay okay" ya fada yana matsa hannuna da yake cikin nasa a kokarin sa na ganin yayi calming dina down amma ko kadan banji hankalin nawa ya kwanta ba. Ya saki hannuna tare da mikewa ya taba wani abu a jikin dashboard din motar sai naga haske ya kawo a jiki, ba wai hasken da zai haska motar gabaki daya ba but just enough to let us see each other. Ya dawo ya zauna tare da juyowa sosai yana fuskanta ta "shinenan?" Nayi shiru bance komai ba ina kara takurewa a waje daya tare da kallon duk wani movement dinsa, Ya dawo ya zauna sosai yana karewa fuska ta kallo, Sai ya lura da hawayen da suke kyalli a cikin ido na yace cikin mamaki "wai harda kuka? Daga duhu sai kuka? Kin fiya shagwaba Safiyya" nayi kokarin gogewa tare da turo baki cikin shagwabar nace "ba kai bane ka kashe fitila kuma ni bana son duhu. Allah kar ka kara kashewa" ya danyi murmushin da ban gane ma'anar sa ba yace "to menene abin toro a duhun in banda dai ke matsoraciya ce, menene zai kama ki bayan ina nan" na yi magana a can kasa yadda ba zai ji ba "kai ne ai bana son zama da kai a cikin duhun" yace "me kika ce?" Na girgiza kaina da sauri "ni babu abinda nace" ya bini da wannan kallon da bana so, nayi saurin duke kaina sai yace "baki da gaskiya, gulmata kika yi ko?" Nace "dama mutum yana gulma shi kadai? Ni da zuciyata muke magana" ya matso yana kara tsare ni da idanuwansa da na kasa cigaba da kalla "waye zuciyar ta ki to? Na dauka nine ai, ta yaya kuma za'a yi magana da ni ban ji ba" yadda yake maganar a hankali ya saka nake jinta tun daga kunnuwana har tafin kafa ta. Na mikar da hannu na da niyyar yi masa shamaki kar ya karaso jikina "kayi alkawari, kar ka manta kayi alkawari, kuma alkawari abu ne mai girma" sai ya zura yatsun sa cikin nawa tare da sauke hannayen namu kasa a tare. Na daga haya hannun na nuna masa karshen kujerar ta daya bangaren "ka matsa can ka zauna, ai kace magana zamuyi, amu iya yi kana can ina nan" ya kalli gurin sannan ya kalle ni tare da tabe baki sannan sake rike daya hannun nawa da dayan nasa "too far.... Ba zamuji maganar juna ba. Ko kinfi son sai muni amfani da microphone wajen hirar? Zance fa nazo" ya karasa maganar yana robbing thumb dinsa a wrist dina. It was just a simple touch, maybe innocent maybe not tunda ban ga zuciyar sa ba but it sent chills down my spine. Nayi sauri na kwace hannun ina gogewa a jikin skirt dina "no touching. You promised no touching" na kwashe dayan hannun shima tare da boye su duk biyun a baya na. Ya jingina kansa a jikin kujerar yana kallona da dariya a fuskar sa, na bata rai "kana sane wallahi. Tsokana ta kake yi wallahi. Dama alkawarin ba da gaske kayi ba" ya daga kafada "da gaske nake mana. Zuwa nayi kawai muyi hira muci kaza. And we can't do that while knocking Daddy might be watching ko?" Nace "to ai ba hirar kake yi ba. Ta ba ni kake yi. WhatsApp.com KAYANMATA CLS WAITLIST WhatsApp Group Invite 5 10:27 Kuma in kana da gaskiya me yasa ka siyo kaza?" Yanzu dariya yayi so sai sannan ace "shikenan yanzu ba zanci kaza ni da matata ba sai da wata manufa. Maybe abun yana ranki ne shi yasa har kika takura kanki haka" na harare shi ban ce komai ba sai ya sake cewa "ki rantse da Allah ba abinda yake ranki ba kenan. The innocent me is just trying to talk" ya fada yana kara matsowa har jikin mu ya na haduwa idonsa tar akan fuskata, gani dama a jikin kofa nake a makale. Na zaro ido tare da saka hannu na biyu a kirjinsa na tura shi baya da dukkan karfina. Bai motsa ba sai hannuna da naji ya sage "ash" na fada ina rike guiwar hannun, "sannu" ya fada yana rike inda na rike din "ciwo kika ji? Bara in yi miki addu'a" sai ya sunkuyo da fuskarsa dai dai damtsen hannuna ya ja hannun rigar sama ya fara hura min iska, sunkuyawar da yayi ya saka gashin kansa yazo dai dai fuskata da wuyana. Kamshin sa naji ya wuce ta hancina ya shige har jijiyoyin jikina, Kuma dai a ido kamar zai yi laushi in an taba. Saukar lips dinsa a cinyar hannu na ne ya saka na dawo daga tunanin gashin kansa, na tura shi baya da karfi kuma da sauri, saboda sammatar sa da nayi wannan karon shi yasa na samu nasarar raba shi da jikina. Na sake nuna masa karshen kujerar nace "ko ka koma can ko in koma cikin gida. Wallahi babu gaskiya sam a lamarin ka yau" ya daga hannu "okay okay naji. Amma na tabbatar miki babu abinda ya kawo ni yau sai tarin gaskiya. Zan koma, amma ta yaya zamu yi hirar kuma?" Ya fada yana komawa can karshen kujerar jikin kofa kamar yadda nima nake. Na sauke ajjiyar zuciya sannan for the first time tun da a shiga motar na shaki numfashin da ya karasa min har cikina. Na dan daga murya nace "in kayi magana kamar haka zanji abinda kace" sai dai kuma sai muryar tawa ta fito da karfi five da yadda nayi niyya. Ya toshe kunnuwansa da hannayensa "wai! Zaki cire min dodon kunne ai" na harare shi na sake maimaita "ba ka da gaskiya wallahi" amma sai stupid zuciya ta take cigaba da jaddamin kyawun da yayi mata duk kuwa da yadda take bugawa da karfi cike da tsoron sa as a man, Sai ma ga ya dauko wata leda karama ya shimfida a tsakanin mu sannan ya dauko bakar ledar da nake tunanin kazar da ya ambata ce a ciki ya dora akai ya bude ledar, wata container ta bayyana transparent, irin wadda ake packaging abinci a fancy eateries. Ya bude gasashshiyar kaza ta bayyana wadda a take kamshin ta ya cika motar, ya bude wasu kananan robobi da suke tare da robar kazar, daya sauce ce itama da take tashin kamshi mai dadi dayar kuma yaji ne irin na masu siyar da suya. Ya sake dauko robar youghurt ya ajiye tare da dan dube dube kadan sannan yace "na manta cups. Zaki iya sha ta bottle din?" Na tabe baki tare da dauke kaina gefe kamar ban ma ga kazar ba nace "ni bana sha. Ba zan ci naman ba ma" yace "ai kuwa da kinyi missing. Kun iya gashin kaji nake gaya miki" ya fada yana gyara zaman sa tare da gutsirar naman da na kara tabbatar da laushin sa, gashi sai mai ko yake yi a hannunsa, ya dangwala a cikin sauce din sannan ya saka a bakinsa ya tauna tare da lumshe ido "hmmm. Kinji dadin kuwa?" Na dauke kai kamar ba shi nake kallo ba tare da tabe baki, "ta yaya zanji dadin tunda bani nake ci ba?" Ya sake daukan wata tsokar ya dangwala a cikin yaji ya kara sakawa a bakin sa yana kallo na yana murmushi, Na kara hade rai. "Har abinci na saka aka yi maka. Amma kaki shiga ciki ballantana ka ci. Shikenan babu komai" ya hadiye tare da korawa da youghurt din sannan yace "okay let's make a deal. Zaki ci kaza ta ni kuma zan karbi abincin da kika shirya min, zan tafi da shi gida ko gobe ne sai inyi warming" na dan kalle shi da alamar tuhuma. "yau gaba daya alkawari kake yi kana karyawa. Kar inci kaki karbar abincin" ya miko min hannunsa "mu daura alkawarin to, yadda ba zan iya kuncewa ba" nature hannun nasa tare da hararar sa '"no touching" sannan na saka hannu na a cikin naman, dama duk yawu na ya gama tsinkewa. Na mika masa hannu "ina nawa youghurt din?" Ya danyi dube dube yace "sai dai muyi sharing wannan, na so in taho da cups da sai mu raba" na dauki robar amma mai makon in saka bakina akan inda ya saka din sai na daga ta na tsiyaya a cikin bakina, saura kadan in kware saboda kallon da ya bini da shi, irin kallon kin raina min hankali din nan tare da na zaki gane kuren ki. Na shaye ina gyaran murya tare da kunshe dariya ta, yace "ni ko?" Yana nuna kansa, "wallahi zaki gane da ni kike" na daga kafada ta ina dariya kasa kasa cikin tsokana "wa ace ka siyo daya?" "Zaki sani, I will not forget this" ya fada yana cigaba da cin kazarsa. Nima cigaba nayi da ci, dan sosai tayi min dadi, daga nan kuma sai muka kama hira, ya sake bani labarin gyaran da za'a yi wa gidan sa da zamu zauna, na fahimci fasalin da moons construction company suka yi proposing yayi masa sosai dan sai kara yaba tsarin yake yi, sannan ya fada min already Mama ta bayar da kwangilar kayan lefe, za'a bawa matar da aka bawa number ta ta kira ni in gaya mata sizes tare da sauran bayanai. Ni kuma sai na bashi labarin dramar da akayi tsakanin Salima da iyayen mu mata akan walimar da nace zanyi, na tambaye shi kuma ko yana ganin zasu yi wani abun da zasu bukaci inje? Sai ya ce Mama dai kamar ba zata yi ba "but am not sure about my aunties, musamman Ummee, kullum neman uzurin da zai kawo ta Nigeria take yi" sai kuma ya amince da shawarar inyi taro na da friends dina kawai dan mufi bonding sosai, "Friends are very important in life, sometimes as important as families" ya danyi shiru sai kuma yace "as for the rest of the family kuma a shawarce ranar da zaki tare sai a shirya musu walima a can gidan, grand walima, kin san iyaye akwai son zuwa ganin dakin amarya, sai suje su wuni a can su ga ko'ina su kuma yi duk abinda suke so. Kinga shikenan ba zasu ke dawowa daya bayan daya ganin dakin amarya ba" ya karashe yana min kallon da bana so. Na dauke kaina amma kuma naji shawarar tasa ta kwanta min, amma ban yanke hukunci ba tunda ina gain ba hurumi na bane ba sai nace "hakan kuma yayi ma'ana sosai. Zan bawa Mommy wannan shawarar inji abinda zata ce" ya gyada kai "do that. Abinda tace din sai ki gaya min. Sai inyi wa Mama magana ita ma inta yarda har suma bangaren su duk sai a hadu a gidan ranar" sai kuma na dan bata fuska "kar fa aje a bata min gida" yayi murmushi "to sarkin tsafta. Akwai compound da zai dauki kowa ai. Duk cin abinci sai ayi a waje. Cikin gidan kuma sai a ajiye masu gyarawa continuously har a gama" Na dan yi shiru ina shan youghurt din da na manta na saka robar akan lips dina, sai yace "there is another thing kuma da nake so muyi magana" na dan juyo ina kallon sa sai yace "what do you think about zuwa Kura?" Na dan bude ido ina kallon sa kirjina yana bugawa "Kura?" Na maimaita cikin mamaki sai ya daga kafada yace "Kura da kwatarkwashi" na girgiza kaina. "Ammie tace kar inje" ya sauke ajjiyar zuciya "haka ne. She was afraid kar su cutar da ke kamar yadda suka yi niyyar cutar da ita. But lokaci ya tura da yawa, zamani ya chanja sosai. I doubt idan wadancan da suka samu sabani da su suna da rai har yanzu ko kuma still suna harboring grudges akan abinda mahaifinsu yayi shekaru kusan 45 da suka wuce. And kamar yadda kika ce Daddy ya gaya miki ranar nan, a ko'ina akwai mutanen kirki akwai kuma mutanen da bana kirki ba. A cikin siblings din Ammie ba zamu rasa na kirkin da zamu jawo jikin mu ba. Ko da daga nesa nesa ne a fara zumuncin in mun fahimci hali sannan sai mu jawo su kusa" na sauke ajjiyar zuciya ina kallon sa amma bance komai ba, sai ya cigaba "and about kwatarkwashi, tun ranar da kika bani labarin iyayen Baba Hadiza, I thought about it, na san irin wadannan fulanin mai gari shi yake basu land su zauna idan sun shigo garin sa, sannan kuma suna bin the same route ne a tafiye tafiyen su, so probably ba za'a rasa descendents dinsu da har yanzu suke wuce wa ta kwatarkwashi ba, zamu iya samun record a wajen dagacin garin, za kuma mu iya bashi cigiyar cewa idan har sun shigo garin a sanar da mu ko a basu number waya su kira. I just want us to do something, I just want you to have them back in your life. Kinji?" Na dan goge hawayen da naji ya fara taruwar min. There is a genuine concern about yadda yake yi min magana that touched my heart. Ya cigaba "Please, at least tell me you will consider it. Ko ba zaki yi yanzu ba" ya gyada kai da sauri ina kokarin mayar da hawaye na, ina missing Ammie sosai and tabbas samun danginta a kusa da ni zai cike min wani gurbin na kewarta. "Insha Allah. Zan yi magana da Daddy akan hakan. Zai ji dadi na sani" yayi murmushi "ina son Daddy sosai" nima na dan yi murmushin sai ya fara tattare containers din da muka ci kazar a ciki sannan ya dauki wipes ya kama hannuna ya fara goge min yana kallona, ban kula shi ba na san neman magana ne sai na dauki youghurt dina na cigaba da sha, sai da ya gama ya goge nasa hannun ya rufe packs din ya mayar cikin ledar tare da bude kofar ya fita, nima sai na ciri wipe din na goge yar karamar ledar cin abincin da ya shinfida duk da ba bashi tayi ba sannan na nannade ta na mayar inda naga ya dauko, a lokacin ne na lura da wata robar youghurt din da take ajiye a kasa. Ya bude motar ya shigo sai na dago ta ina hararar sa. Yayi murmushi bai ce komai ba sai na ce "baka da gaskiya na gaya maka "yayi yar dariya "ai baki ji nace dama guda daya na siyo ba ko? So nake in mun shanye daya sai mu sake shan dayan" na sake hararar sa tare da mika masa guntun wanda nake sha na dauke wancan da ba'a bude ba. Ya ajiye yana gyara fuskar sa kamar wanda zai yi wata serious magana yace "akwai sauran abu daya kuma mai muhimmanci da nake so muyi magana akai" na nutsu nima ina mayar da hankali na sosai a kansa, sai ya kama hannuna na ya rike yana kallon cikin ido na yace " want to confess something. Kawai dai kuma bansan me zan ce miki ba. I don't know how to tell you, ina jin nauyin ki sosaj" naji gaba na ya fara faduwa, menene wannan zai gaya min haka. Na tattaro courage dina nace "menene?" Ya danyi shiru yana kallon fuskata sannan yace "youghurt din da muka sha, na mayar da na baki ciki". Na zaro ido yayin da ya kyalkyale da dariya, na dan dake shi a kafada "kai kazami ne Allah kuwa, ba zan kara cin abinci da kai ba" dariya sosai ya kama yi, irin dariyar da ban taba ganin yana yi ba, nima dariyar na fara taya shi totally forgetting the tension between us, "Allah zaka gane kuren ka" na fada cikin dariya, a cikin dariyar ne kuma na jini a jikin sa, na sa jawo ni yayi amma ban ji sanda ya jawo nin ba. Nan take dariya ta ta tsaya, bugun zuciya ta ya dawo da karfin da yafi na dazu, na fara kokawar raba jiki na da nasa ta hanyar saka hannu na daya in tura shi sai ya rike hannun a cikin nasa hannun guda daya, dayan hannun kuma ya kara riko waist dina tare da hade jikin mu sosai. Idanun sa akan fuskata yana bin kowanne feature na fuskar da kallo kamar me neman haddace komai. Babu sauran dariyar a fuskarsa. "Ka cika ni" na fada murya can kasa, bana jin dadin kallon da yake yi min sam, na sauke ido na kasa a kokari na na daina kallon cikin idonsa "anki din" ya fada yana wasa da yatsun hannun sa a cikin nawa, nayi kokarin kwache hannun sai ya sake rike shi. "Ka sakar min hannu na" na fada ina jin abinda yake min a hannu har cikin tafin kafa ta, "na karfi ne, in kina da karfi ki kwata" ban ce komai ba kuma bana jin ko nayi magana muryar zata fito saboda yadda numfashi na yake yin sama a lokacin da hannunsa ya bar yatsun hannuna ya biyo hannun har zuwa wuyana. "You promised" na fada a hankali, "I lied" ya bani amsa a can kasan makogwaronsa a lokacin da hannunsa ya karaso fuskata, na dago idona saboda jin iska mai dumi da nayi a fuskata, idanuna suka sauka a cikin nasa, hancinsa a saman nawa muna shakar numfashin juna, kamar yadda yake futar da numfashi mai zafi na tabbatar nima haka ne, na rufe idona dan ba zan iya daukan abin da nake gani a cikin idonsa ba. And then he kissed me……. A tsorace na kwace jiki na daga nasa bayan mintunan da ban san adadin su ba. Ban san ya akayi ba sai gani na nayi na tsallaka seat din gaban motar na kuma dunkule a waje daya jikina yana karkarwa, acn motar tana sauka a naked fatar bayana da ba zan iya tuna sanda zip din rigar ya cire ba ballantana yadda akayi rigar ta kusa barin jikina completely. Sai da nayi ta mayar da dogayen numfashi kafin in dan samu in daidaita tunani na sannan na fara kokawar yadda zan mayar da riga ta, sai dai zip din yaki cooperating, yaki jera kansa ballantana in zuge shi, ko kuma karkarwar da jiki na yake yi ne? Na san yadda akayi tafiyar ta fara, amma ban san yadda akayi tafiyar ta yi nisa sosai ba sai da naji lips dinsa a inda ban taba tunanin zasuje a yau ba sannan na dawo hayyacina. Hannuna har ya kage saboda kokarin gyara rigar amma taki gyaruwa, kamar zanyi kuka. Na kuma kasa daga idona ballantana in kalle shi. Ina dai jin sa jera numfashi a baya, maybe trying to calm himself down kamar ni. Ni bana jin ma zan iya kallon sa a yau dai kam. Naji muryarsa kamar wanda yake magana daga can nesa "Hey! Tsaya in gyara miki kar kiji wa kanki ciwo" na kara takurewa a kasan kujerar tare da rufe fuskata da hannayena biyu "ya Rabbi" na fada a hankali. Naji motsinsa ya taso sai na kara makurewa kamar zan shige karkashin kujerar "ki tsaya, rigar zan gyara miki" ya fada still not sounding like himself. Na kife fuskarsa a kan seat din kujerar ban kalle shi ba kuma banyi magana ba. Naji ya sake sauke wata ajjiyar zuciyar sannan ya bude kofar motar ya fita sai kuma naji ya bude seat din driver ya shiga sannan naji hannun sa a baya na ya mayar min da bra strap, duk da naji bai saka dai dai ba banyi complain ba sai kuma ya hada zip din rigar ya zuge. Ban ce komai ba sai na dago hannuna daya na mika masa, yar dariya yayi kadan sannan naji ya saka min dankwalina a cikin hannun, ban kalle shi ba na daura, daurin da na tabbatar bashi da maraba dana tababbu, sai na kuma mika masa hannu na sai ya saka min mayafina, na lulluba a jikina ba tare da na kalli mayafin ba ballantana in ga ko na saka dai dai ko akasin haka, ina jin sa yana dariya kasa kasa amma a raina nayi kwafa ban ce komai ba dan ba zan iya cewa komai ba. Na bude kofar motar ba tare da nace komai ko na kalle shi ba na fita, sai da naji kafata ta taka duwatsu a kasa sannan na koma na zauna akan kujerar tare da cewa "auch!" Yayi saurin cewa "menene?" Ban amsa ba sai na kuma mika masa hannu na, bai gane abinda nake nema ba sai da ya kuna fitila ya duba baya sannan ya miko min takalma na yana dariya. Nayi kwafa a fili na saka takalman sannan na karasa fita na bar masa kofa a bude. Na jishi ya fito daga motar ya biyo bayana yana dariya kasa kasa, ya danyi kokarin gyara min mayafina sannan yace "ga wayarki, ko kin barmin" na mika masa hannu bance komai ba sai ya saka min ita a cikin hanun, daga nan na kara sauri har na je gate, ya bude min kofa na shiga sai ya rike mayafina "Please look at me mana" na girgiza masa kai da sauri sai ya saki mayafin yace cikin tsokana "sai na sawo gobe" ban ce masa komai ba na kara sauri zuwa ciki, sai da na shiga sannan naji motsin rufe kofar gate. Shirun da naji gidan yayi ya saka na fahimci kowa a gidan yayi bacci, na sauke ajjiyar zuciya cikin jin dadin hakan dan gani nake yi kamar duk wanda ya kalle ni zai fahimci abinda ya faru, musamman in aka ga lips dina. Na saka hannu ina goggoge su ina jin yadda suka zama puffy, Allah kadai ya san lokacin da na bata a cikin motar nan tare da mutumin nan. Nayi kwafa. Da ni yake maganar. Har da wani cewa sai ya dawo gobe ko? Zai ga gobe ganin idon sa. Har lokacin jiki na rawa yake yi. Na zauna akan kujera trying to get the scene and the feelings out of my head. Karar waya ta ya saka na dan zabura kadan. Na duba naga sunan sa, he must be kidding me, me zai ce min kuma? Sai kuma nayi tunanin o wani abun na manta mai muhimmanci, a dauka na saka a kunne na ban ce komai ba sai yace "abinci na. Ki kawo min abinci na" bance komai ba na katse kiran, Ni ina zanga abinci a gidan nan yanzu? Amma duk da haka sai na duba kitchen, cikin ikon Allah na samu warmers kanana a jere a gefe, na bude na tabbatar abincin da Esther ta hada mishi ne, na dauko basket na jera na bude fridge naga drink din da nake tunanin shi ta hada wa sannan na rufe basket din. Sai dai ni nasan ba zan iya komawa waje gurin sa ba. Na hau sama dakina na tarar da Salima tana kallo a tv tana ta kyalkyala dariya. Ina shiga ta dago kai tana kallo na sai kuma ta kwashe da dariya, "wannan daurin fa?" Na taba kaina sannan nace cikin muryar da naji kamar ba tawa ba "yanzu dankwalin ya kunce a kitchen, ban ma san ya daura shi ba". Cikin tsokana tace "ai na dauka sai dai a aika miki da kayan ki" ban kula ta ba na cire mayafin da dankwalin sai kuma nayi sauri na duba a madubi dan bana son ta ga wani abu kuma again, casually nace mata "dan Allah Salima ko zaki kai masa abinci waje? Yana mota" ta mike zaune "au bai ci abincin ba? Esther tayi ta sintiri tana neman ki ai, na dauka an kai masa" nace "bai ci ba. Wai tafiya zai yi da shi. In na fita kuma tsayar da ni zai kuma yi. Dan Allah ki kai masa. Gashi can a kitchen" ta sauka daga kan gadon ta fita tana maganar da banji abinda tace ba. Tana fita na zauna akan kujera tare da dafe kaina. Wannan aure anya kuwa? Wannan mutum ya zanyi da shi? Ina son sa sosai amma Allah ya sani ina matukar tsoron abinda aure ya kunsa, abinda kuma na tabbatar ba zai iya daga min kafa akai ba. Da dai kuma ace irin na yau ne kadai za'a ke yi ana bari da da sauki sauki. Na rufe idona tare da kwanciya akan kujerar ina kokarin daidaita tunani na. A haka Salima ta dawo ta same ni bakin ta har kunne, ta daga min rafar sabbin kudi da aka bata tana rawa, sai kuma ta zauna tare da cewa "an bani amanar ki. Ance in kula da ke sosaj" na dan yi mata murmushi kadan. Ta sake cewa "I thought ba zai sakar min fuska ba saboda Yaya Mukhtar. Amma yayi min fara'a kuma har ya bani kudi " na mike nace mata "ke ba Mukhtar ba ce ba kuma Mukhtar ba ke bane ba" daga haka na shiga toilet dan bana son ta kara ambatar sunan Mukhtar especially not now da nake cikin tunanin yadda zan iya fuskantar aure na saboda abinda yayi min. A toilet na kimtsa jiki na nayi alwala na fito zan yi sallah sai take gaya min twins ma sun shigo nema na. Na jinjina kai kawai, tunda akayi daurin auren nan bamu yi magana da su ba kuma a zuciya ta ina son muyi magana dan mu samu fahimtar juna. Sai da na idar da sallar sannan na sake fita na duba Daddy na tabbatar yana baccinsa peacefully sannan a duba Mommy ita kuma na ga bata yi bacci ba tana kallo kuma tana waya, na fahimci da Safina suke wayar sai nayi mata sai da safe na koma dakina nayi shirin bacci. Ina jin waya ta tana kara da sound din Muhammad sai na dauka sannan na saka ta a silence, haka yayi ta kira na, ina kallon sunan na sa ina murmushi amma ban dauka ba. Sai kuma ya turo min message "Please come online" sai da na ja aji na kadan sannan na hau. "Yanzu ba zakiyi min magana ba? So nake fa kawai inji muryar ki. Dan Allah ki dan yi min magana mana ko ba kya so inyi bacci yau" "Uhmm" "Yanzu anan ma ba zaki yi min magana ba? Wai laifin me nayi ne?" "Karya alkawari" "Dama sanda nayi alkawarin ba har zuciyata ba ne ba. Allah ma ya san ba har zuciyata bane ba. Though ban dauka cewa I will take it that far ba. But you are very beautiful and sweet. I lost control" Na danyi murmushi bance komai ba. Ya sake turo wani "Can we meet tomorrow? Maybe at the Oasis?" “Nooo” “😂. I promise magana kadai zamuyi. I will not touch you" "Goodnight Baby" "Good night. And I love you" "I love you too" Na tura masa tare da lumshe ido ina jin sonsa tare da wani sabon feeling daban da ban san shi ba, mai hade da tsoro suna gauraye zuciyata. Washegari nayi maganar walimar da Gidado ya bani shawara tare da Mommy, ta amince cewa hakan din dai dai ne, amma direct ta gaya min cewa babu wanda zata gayyata daga side din ta except Hajiya da take dole. Na fahimci haka kuma banji komai a raina ba dan nasan it's for the best. Sai kuma naji na sake jin kewar dan gin Ammie. Hakan ya saka ina zuwa gurin Daddy na gaya masa maganar da muka yi da Muhammad jiya. Sai naga yaji dadin maganar sosai musamman maganar dangin Baba Hadiza. "Yaron nan yana da hankali sosai. Amma a shawarce ku bari sai bayan bikin ku in hankali ya kwanta sai kuje". Sai na sake yi masa maganar Mustapha "Daddy yaushe zaka dawo da Mustapha?" Ya dan kalle ni yace "sai kin bar gidan. Zai dawo, amma sai kin tafi gidan mijinki". Da yamma Aunty Hajjo ta dawo gidan kamar yadda tayi alkawari. A tare da ita akwai another guest. A little human being. Ta miko min shi "rike min wannan yaron Safiyya ki huta. Ya zama kato duk ya gajiyar da ni" na mika hannu zan karbe shi sai ya makale kafada yana kara rike rigarta. Na daga kai na kalle ta sai tayi murmushi "kyuiya fa yake yi dama. But in kika dauke shi zai hakura" na sake mika hannu na dauke shi ina jin yadda yayi nauyi. Yayi ta bin fuskata da kallo sai kuma ya turo baki yana jera ajiyar zuciya. Ya kumbura fam kamar zai fashe. Aunty Hajjo tayi dariya "in kina da sweet je ki bashi. Amma ba me zaki sosai ba" Salima da ake yi a gabanta ta zo ta shafa kansa tace "cute boy" ai kuwa a take ya fashe, ya kwarara hun da ya cika gidan gabakidaya, sai ga mutane sun fara fitowa, Mommy ta sauko daga sama sai na mika mata shi kamar zanyi kuka, ta karba ta jefa shi sama ta chafe sai ya kara sound din kukan. Sai ga Hassan nan ya shigo shima ya karbe shi "Mommy dan waye wannan?" Mommy ta kalli Aunty Hajjo tace "dan Hajjo ne" Hassan yayi murmushi '"ban taba ganin baby a gidan nan ba". Farko da Hassan ya karbe shi sai yayi shiru, Aunty Hajjo tace ya dauka Abdul ne, amma kuma sai yake ta kokarin leka fuskar Hassan din, suna hada ido kuwa ya sake wage baki da kukan da yafi na baya karfi. Hussain shima yazo ya gwada tasa basirar amma Junior yaki, sai ga Daddy ya aiko wai waye ya cika masa gida da hayaniya? A kai masa shi. Na sunkuyar da kaina kasa dan na san ya fahimci waye, tunda Aunty Hajjo tace tare suke da uncle Sufyan kuma yana wajen Daddy din, sai Hassan ya dauke shi ya tafi da shi can. Sai kuma muka ji shiru. [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: Da yamma Aunty Hajjo ta dawo gidan kamar yadda tayi alkawari. A tare da ita akwai another guest. A little human being. Ta miko min shi "rike min wannan yaron Safiyya ki huta. Ya zama kato duk ya gajiyar da ni" na mika hannu zan karbe shi sai ya makale kafada yana kara rike rigarta. Na daga kai na kalle ta sai tayi murmushi "kyuiya fa yake yi dama. But in kika dauke shi zai hakura" na sake mika hannu na dauke shi ina jin yadda yayi nauyi. Yayi ta bin fuskata da kallo sai kuma ya turo baki yana jera ajiyar zuciya. Ya kumbura fam kamar zai fashe. Aunty Hajjo tayi dariya "in kina da sweet je ki bashi. Amma ba me zaki sosai ba" Salima da ake yi a gabanta ta zo ta shafa kansa tace "cute boy" ai kuwa a take ya fashe, ya kwarara hun da ya cika gidan gabakidaya, sai ga mutane sun fara fitowa, Mommy ta sauko daga sama sai na mika mata shi kamar zanyi kuka, ta karba ta jefa shi sama ta chafe sai ya kara sound din kukan. Sai ga Hassan nan ya shigo shima ya karbe shi "Mommy dan waye wannan?" Mommy ta kalli Aunty Hajjo tace "dan Hajjo ne" Hassan yayi murmushi '"ban taba ganin baby a gidan nan ba". Farko da Hassan ya karbe shi sai yayi shiru, Aunty Hajjo tace ya dauka Abdul ne, amma kuma sai yake ta kokarin leka fuskar Hassan din, suna hada ido kuwa ya sake wage baki da kukan da yafi na baya karfi. Hussain shima yazo ya gwada tasa basirar amma Junior yaki, sai ga Daddy ya aiko wai waye ya cika masa gida da hayaniya? A kai masa shi. Na sunkuyar da kaina kasa dan na san ya fahimci waye, tunda Aunty Hajjo tace tare suke da uncle Sufyan kuma yana wajen Daddy din, sai Hassan ya dauke shi ya tafi da shi can. Sai kuma muka ji shiru. Daga nan Aunty Hajjo suka cigaba da maganganun su da Mommy. Ranar lissafin siyayyar kayan daki suka fara, Mommy tayi min maganar kaya na na gidan Mukhtar sai na gaya mata abinda nayi da su, ta tsaya kawai tana kallona sai kuma ta girgiza kanta suka cigaba da maganar su. Har Mommy ta dauko takarda zata fara list na kayan da za'a siya sai Aunty Hajjo ta bada shawarar a bada kwangila kawai, a samu kamfanin da suke interior design a basu kwangilar komai, za'a hada ni da su yadda zan ke gaya musu duk abinda nake so su kuma suna taimaka min wajen zabe da kuma siyowa "in muka yi haka mun huta, kuma tunda aikin sune hardly su manta wani abu". Mommy ta amince da shawarar ta. Ni dai na barsu da wannan na koma sama zanyi sallar azahar. Ban sauko ba har akayi la'asar nayi na shiga toilet nayi wanka ina fitowa sai naga Junior shi kadai a zaune a kan gado na. Na sam Aunty Hajjo ce ta kawo min shi. Na durkusa a gaban gadon ina kallon sa yanata wasa da toy dinsa, sai kuma ya juyo yana kare kin kallo, a karshe yay deciding cewa bai sanni ba sai ya turo baki ya fara ajjiyar zuciya idonsa ya ciko da hawaye. A hankali nace "hey there! Remember me?" Ya cigaba da kallo na nima sai na samu damar are masa kallo. Yayi fari sosai yayi kiba kamar zai fashe, fatarsa kamar zaka taba jini ya fito, komai a jikinsa yana nuni da yadda yake cikin kwanciyar hankali. Idonsa yana nan irin na ubansa amma sauran features din sa ba zaka kalla direct kace nawa bane ba sai dai in kallon kurilla zaka yi masa. Sai na tuna da chocolate din da Abdul ya kawo min ranar nan naki sha na dauka shi za'a aura min, na bude inda na ajiye su na dauko na nuna masa ya miko min hannu da sauri tare da yin gwarancin da ban gane ba "acici, har yanzu kana nan da cin ka ashe Adam" na karasa na bude masa na mika masa, garin karba ya hantsula baya ya kwanta, sai na jashi na tare shi da pillow, sai ya fasa kukan ya kama shan sweet. Mun jima tare ina ta vi masa hira shi kuma yana ta shan sweets dinsa, har labarin aure na sai da na bashi da kuma yadda nake son angon, ya bata jikinsa gabaki daya ya kuma bata bedsheet din, sannan daga baya ya rarrafo jikina nima ya bata ni da chocolate din. Aunty Hajjo ta shigo tan kallon mu, yana ganin ta ya fara mika mata hannu yana murna, ya rike haba "oh Allah, haka dama ake renon Safiyya" nayi murmushi bance komai ba. Ta mika hannu ta dauke shi tayi toilet da shi da sauri tana cewa "ni dai ba zaka bata min jiki ba. A toilet naji su suna ta babbaka dariya sannan suka fito ta gyara masa jikinsa tas. Na mika masa hannu sai ya makale, tayi dariya, "sweet din ki ta kare aj" nayi hanyar fita tana cewa "mu zamu tafi. Ba lallai mu dawo gobe ba sai dai idan da akawai wani abu mayi waya" har ta kai bakin kofa na ce mata "Aunty Hajjo" ta juyo tana kallona nace mata "thank you" ina kallon Junior da yake ta kara shigewa jikinta yana tunanin daukan sa zanyi. Tayi murmushi tana shafa kansa tace "no. Thank you. Mune da godiya. He is nothing but a blessing to us". Bayan sun fita sai na bisu a baya, ina jin kamar in ie ince ta bani dana amma na san hakan shine dai dai a gare shi. Ina tsaye akan barandar naga Abdul ya shigo, daga inda nake na hango yadda Junior yake murna da gain sa, shima cikin murnar ya karbe shi tare da kissing Cheeks dinsa sannan suka fita. Salima kamshin take yi. An kawo lefe. Maza ne suka kawo kamar yadda Daddy ya bukata, muma anan mazan ne suka karba anan falon Daddy, suka kuma saka tariyar ta kasance sati daya bayan kawo lefen. Sai da suka yafi sannan aka shigo dasu cikin gida mata suka gani. Ni kam na san kusan komai da yake ciki dan da yawa daga cikin kayan ni na zaba tare da taimakon wadda suka bawa kwangilar. Komai na lefen yayi min kamar yadda komai yayi min a cikin kayan da designers din gidana suke siya. Duk da ba'a gama aikin gidan ba amma na basu plans din gidan sun san yawn dakunan da kuma sizes din su da komai, dan haka ta haka suke siyayyar su. A lokacin problems dina guda biyu ne kawai. Na farko jikin Daddy da yake kara lalacewa kullum, gashi kuma wai zan tafi in barshi a cikin wannan halin. Sai na bivu angon nawa da yake kara rikice min kullum. Har sai da nace ina ma ba'a daura auren nan ba an bari sai an gama shirin tukunna? Zuwa lokacin har cikin raina tsoron kebewa da shi nake vi. Hakan kuma ya kara min tsoron abinda zai kasance a cikin auren namu. Ko ya na tuno abin sai toro ya kamani. Har tashi nake yi cikin dare in roki Allah ya yaye min tsoron mijina da na fara. Ba wai shi nake tsoro ba, ina son sa sosai kuma na yarda har cikin raina ba zai cutar da ni ba, amma ko yaya nay imagining kasancewa da shi a matsavin mata da mili sai na tuna ranar nan, ranar da tafi kowacce rana baki a rayuwata. Sai na tuno pain din, sai na tuno darkness din. Sai kuma na tuno fear din. And it kept me up at night, Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Sixty Five: The Wedding Tunda satin bikin ya shigo abubuwa suka kara rikice min. Duk da dai aunty Hajjo tana taimaka min da abubuwa sosai dan Mommy ta zama very moody a cikin kwanakin nan, ta daina fadan ta ma daina magana sosai and it broke my heart to see her like that amma sai in taushi kaina da gayawa kaina cewa bani na saka ta a cikin damuwa ba. Ina dai iyakacin kokarin ganin nayi involving dinta a komai ko da kuwa ta hanyar bata update ne akan duk abinda ake ciki, in ta bada shawara kuma ina kokarin gain nabi dan in faranta mata ko yaya ne. Amma na san zuciyar ta tana wajen yayan ta. Bata taba yi min maganar Safina ba nima ban taba yi mata ba, haka Muhammad, bai taba yi min maganar ta ba nima ban tambaye shi ya suke ciki ba, At a point da abubuwa suka yi min yawa sai da na gayawa Muhammad ko za'a kara sati daya ne? Dan har lokacin masu gini ba su gama finishing ba ga masu saka kaya suna jira, ai kuwa a take yaje ya saka Ya Amen a gaba ya hana shi shakar numfashi mai kyau har sai da suka gama komai in two days sannan ya bar shi ya huta. Sai masu kaya suka fara aikin su, saboda kurewar lokaci haka suka yi aikin nan day and night, na tattara twins na tura su gidan dan su tabbatar anyi komai yadda ya kamata. Da suna can din ma ban kyale su ba ko da yaushe muna waya ina jin abubuwan da aka kawo da kuma a inda aka saka komai, sai kuma su yi min video su turo min in gani dan in tabbatar da cewa abinda na ce ayi ne kuma an saka shi a inda ya dace. Kuma interior designers din sunyi kokari sosai gaskiya. Few things ne naga an samu kuskure akai dan haka banyi dragging ba sai kawai na barsu tunda dan Adam tara yake bai cika goma ba. Aunty Hajjo ma kullum sai taje gidan taga progress din aikin, in da gyara tayi musu, at a point uncle Ahmad ma yaje ya ga komai kuma ya bada nasa shawarwarin. Sosai kuma nake jin dadin yadda komai yake turning out, sosai kuma nake kara investing in making my home as luxurious as I can dan a raina ina ganin nan ne gidan da zanyi mafi yawa daga cikin rayuwata a ciki, gidan da zan haifa kuma in reni yayana. Gidan da zan kira gida na. In three days suma suka gama saka komai da jera komai sannan aka gyara gidan tas aka rufe. Ranar da aka gam aikin, ranar Alhamis kenan, twins suka dawo gida da rana suka tarar da ni tare da Muhammad a harabar gidan mu amma daga side muna zaune akan kujeru sai suka karaso suka gaishe da Muhammad sannan suka gaya mana cewa wai sun kama daki a gidan, yanzu ma kayan su suka zo dauka. Muka yi dariya Muhammad ya ce "to Allah ya sa ba dakin Haidar kuka kama ba dan tun dadewa yace shima ya kama daki" Hassan yace "ko dakin sane tunda mu biyu ne shi kuma shi kadai dole ya hakura ya bar mana, in ba haka ba kuma sai a gwada karfi aga wanda zai kayar da wani" aka sake dariya suka shige, sai nabi bayan su da kallo ina jin dadin yadda suka yiwa Muhammad magana, they have been quite about the whole issue kuma na san an saka su a tsakiya ne, though ni ban taba zama na tambaye su ra'ayin su ba kawai ina involving dinsu ne a cikin abubuwa. Bayan sun wuce Muhammad ya yi clicking fingers dinsa a kusa da fuskata, wannan ya dawo da ni hayyacina na juyo ina kallon sa sai yace "ina kika tafi?" Nayi murmushi "ina nan" yace "a'a, kin bi twins dai kun shige gida kun barni anan" na sake murmushi kawai. Tunda satin ya kama na koma shiru sosai. Magana ma kadan kadan nake yin ta dan abubuwa ne da yawa a raina. Ina son muhammad ina son auren sa amma kuma ina tsoron auren sosai, kuma bana son rabuwa da Daddy. Sannan kuma ga missing Ammie da nake kara yi sosai a kwanakin nan, duk da cewa uwa uku nake da ita a yanzu amma babu wanda zai iya replacing gurbin uwa a zuciyar yarta. Muhammad tun yana tsokana ta yanzu har ya bari, tunda in ya tsokane ni ma ba kula shi nake yi ba. Sai dai ya shigo mu zauna yayi ta min hira ina amsa masa sama sama, An gama tsara komai na yadda bikin zai kasance, kamar yadda Daddy ya bukata ya kuma cigaba da insisting, baya son duk wani abu da zai jawo attention din mutane, ina ganin kuma hakan da yayi ta fada ne ya saka suma gidan su Muhammad ba su shirya wani shagali babba ba. Ya dai ce min zasu yi wuni a gidan kakannin sa ranar friday. Ni ma kuma a ranar Friday din ne zanyi taron da na shiryawa friends dina "Fiyya's Sourie" na kira taron, Muhammad ne ya kama mana inda zamu yi taron ya kuma biya komai, Mufida kuma ta aiko min da gudummawar sovenniers masu tsada da za'a raba wa mutane, da ma na karbi number dinta a hannun Muhammad tun a week to taron muni magana kuma na aika mata da cards guda ashirin nace ita da cousins din su mata. Salima ma tayi wadansu sovenniers din. Daga taro na kuma sai walima da za'a yi ranar Saturday, ranar da za'a kai ni gidan Muhammad. Ita kuma walimar a gidan na wa za'a yi ta a harabar gidan, both family na da na Muhammad zasu yi attending a lokacin ne kuma danginsa zasu ganni, kowa kuma zai samu damar ganin gidan amarya. Muhammad ne ya kawo shawarar kuma aka karba, amma kullum in muna maganar sai nayi masa mitar zai saka a bata min gida, Dan sosai nake ji da gidan nan nawa shima kuma ya sani. Ya kance "ni kam in aka bata gidan nan ina jin ba za'a barni in vi bacci ba" Na dago kai na sake kallon sa dan jin da nayi a jikina cewa kallona yake tayi, muna hada ido na sake mayar da kaina kasa ina yin murmushi sai yace "Please Piya. Ki rufa min asiri ki dawo dai dai. Ni ban saba da wannan ba gaskiya" nace "zaka saba da ita ne ai a hankali" ya girgiza kai "no. Ba zan saba da ita ba. Zan dai dawo da Piya ta ko da karfi ne. Allah dai ya kaimu jibi" a haka ya gaji da shiru shiru na ya yi min sallama ya tafi amma ace zai sake dawowa da dare ya kawo min sako. Na tashi na koma gida. Already gidan mu ya fara cika da yan'uwan mu da suka fara zuwa daga Kano. Cousin din su Daddy da muke kira da gwoggo Hauwa tazo tare da yayanta uku da kuma surikarta. Matan kanin baban su Daddy ma sunzo su biyu. Kanwar babarsa ma wadda take kamar kaka a wajen mu a yanzu ita ma haka ta matsa sai da aka taho da ita tare da matan yayan ta su uku tunda ita yayan ta duk maza ne, Sauran yan'uwa kuma sai washegari muke saka ran zuwan su, Ina shiga tun a falo suka dasa tsokana ta, "'Amarya wanna sheki haka da kike yi duk na amarcin ne?" "Amma kuma ta rame fa" "tsoron auren kike ji?" "To ko dai a fasa ne?" Na juya ya zabga wa wadda ta fadi haka harara, abokiyar wasan mu ce da ma, tayi dariya tare da fadawa goggo Hauwa da take zaune a gefe "harara ta tayi, wallahi goggo harara ta tayi" na sunkuyar da kai kamar ba ni nayi ba na zauna a gefen gwoggo nace "sharri zaki yi min? Ai Allah yana kallo kuma zai saka min" Hasina tace "ni ma na ga hararar fa. Kuma yanzu ma daga gurin angon take, ai na hango su sanda naje ba da sako waje" goggo Hauwa tace "kika je bada sako ko kika je tsegumi?" Ta juyo tana kallona tace "wai so take ta ga wanda yafi Mukhtar da har kika rabu da Mukhtar kika aure shi" Salima da take kwance a gefe ta tashi tace "ai kam dai in kyau ne yafi Yaya, kuma yana da kirki sosai, ga kudi, baku ga motar da yake hawa ba" Hasina ta saki baki tace "lahh ka ga yarinya mai gudun dangi? Nawa ya baki?" Suka sake yin dariya sai gwoggo tace "ni kam ba zance nafi son sa akan Mukhtar da yake da na ba. Amma ina musu fatan alkhairi. Allah ya sa albarka a gidan auren su ya sa mutu ka raba" a hankali nace "Amen" Hasina ta sake cewa "aah gwoggo wallahi Ameen ta ce, ba zaki bari mu mu amsa ba?" Haka muka cigaba da zama a tare muna ta hira, naji suna ta tambaya akan Safina wai basu ganta ba ko sai gobe zata shigo? Su a gain su tunda a garin take aure ai ya kamata a ganta actively a cikin shire shiryen bikin ba wai sai ranar taron zata zo ba. A lokacin na kara fahimtar cewa ba su san waye na aura ba kuma bana jin ko sun ganshi zasu gane shi in dai ba fada musu akayi ba. Watakila zasu sani nan gaba. Watakila kuma akasin haka. Wata kila idan suka sani zasu san complete labarin kuma su goyi bayana, watakila kuma ba zasu fahimta ba zasu zage ni. But in whatever case, I don't care. Anan muka ci abincin dare tare, wadanda basa kusa ma duk suka dawo falon aka hadu aka ci abincin tare, Esther wadda already ta hada kayanta kamar ita za'a yiwa auren ta na ta hidima da mu tare da sababbin yan aikin da aka kawo su uku, Bayan mun gana cin abincin na kira Salima da Hasina da Hafsat muka tafi dakina nace su taya ni hada kayana, Ko kuma ince su hada min kayana, Dan zama nayi kawai ina kallon su suna hadawa ina jin babu dadi a raina, dan lokacin auren Mukhtar babu abinda na dauka a cikin kayana dan ban ma yi tunanin zan yi dadewar da nayi a gidan sa ba. Kayan gurin Ammie gabakidaya na dauka dan ba zan iya bayar da ko daya daga ciki ba. Kayana kuma na dauki wadansu da nake so sauran kuma gabaki daya nace bayarwa zanyi. Ai kuwa su da suke gurin su suka fara zaba, nace "idan kuka dauki da yawa to babu ku a wadancan kayan" Hafsat tace "wadanne kayan?" Nace "ba zan fada ba, amma in dai kuka dauka da yawa babu ku a wadancan" sai suka rarrage, daga nan nace su fifftar su raba wa dangi dan sun fi ni sanin dangin. Ai kuwa haka suka sha rabo, gida gida, duk wadda kaya na zasu iya yi mata sai da ta samu. Sai na bar su suna rabon kayan na tafi gurin Mommy na gaya mata kudiri na "Mommy kayan can na lefe da aka kawo daga gidan uncle Ahmad, ki rabar wa da mutane, duk yan'uwa a raba a bawa kowa, komai da komai, har akwatunan" ta tsaya tana kallona sai na daga kafada nace "babu abinda zanyi da su Mommy, ga wannan lefen da aka kawo, ga dinkunan da nayi, ga kuma kayan da already nake da su". Ta gyada kai tace "shikenan, za'a bayar", Itama haka ta zauna ta rabar da kayan tas, dangin uwa da dangin baban Daddy kowa sai da ya samu, ma'aikatan gidan mu both Kano da Abuja, hatta masu gadi da drivers sai da Mommy ta basu wani abu a ciki. Amma bata bayar da kayan kwalliyar ba sai yace in tafi da su gidan Muhammad saboda baki yan uwansa in sun zo. Na amince da abinda tace, sai ta hada da kayan kwalliyar da kayan lefen da aka kawo daga gidan su Muhammad da kuma kayana da na hada na gida wadanda zan tafi da su ta bawa su Salima Hassan ya kai su suka kai min gidan Muhammad. Ni dai tunda muka yi maganar kaya da Mommy ban kuma bin ta kan su ba, sai dai duk wanda yazo yayi min godiya sai inyi masa murmushi kawai. Da dare Muhammad ya dawo kamar yadda yace zai dawo. Ina tare da Daddy ya kira ni yace yazo yana waje a mota. Na dan j faduwar gaba amma na danne na saka hijab dina na fita. A motar na tarar da shi a zaune a seat din driver sai na zagaya na zauna a gefen sa, na gaishe shi yayi shiru bai amsa ba sai na dago kai muka hada ido na sake mayar da kaina kasa, ya kira sunana "Safiyya" na dago kai da sauri dan ba zan iya tuna ranar da ya kira sunana haka ba. Sai ya juyo ya kama hannayena duk biyun ya rike "look at me" na sake dago kai muna kallon juna "me yake damun ki?" Na dan kirkiri murmushi "ni kuma? Nothing fa. Kawai abubuwa ne dai suka dan yi min yawa" ya girgiza kai "ban yarda ba. Ba zaki fada min ba?" Na sake mayar da ido na kasa ina jin kamar zanyi kuka. "Ba kya son rabuwa da Daddy? Shine damuwar ki" nayi saurin gyada masa kai tunda hakan yana cikin damuwata. Yayi ajiyar zuciya "ba zaki rabu da Daddy ba kinji? Insha Allah kullum zamu ke zuwa muna gaishe shi. Nayi miki wannan alkawarin. Ki saki ranki ki daina damuwa kinji?" Na sake gyada masa kai sai yace 'to kiyi min hira. I really miss the sound of your voice " na danyi murmushi nace "to me zance? Dazu ma ba muni magana ba" yace "nayi magana dai. Ni kadai nayi magana ta dazun ma. Kuma na san gobe ba lallai in samu ganin ki ba. Ko inzo in kai ku gurin gyaran gashin?" Na girgiza kai "muna da yawa ai, ba zaka ji dadin shiga cikin mu ba. Hassan sai ya kaimu ko mu dauki driver" ya dan yi murmushi "ko dai kina kishin kar a gane miki miji?" Na harare shi tare da kwace hannuna in kishin nake yi ma ai babu laifi Miji na mai kyau ne kuma ina son sa" yaji dadi sosai sai ya saka dan yatsa ya dago haba ta yana kallon cikin ido na for some seconds sannan yace "kina da kyau sosai Piya. Ina son ki sosai",. Na danyi murmushi sai yace "I am glad ba za'a yi taron da maza ba, yadda kike ta kara kyau din nan bana so maza su ganki ballantana ace kinyi kyalliya" na dan yi dariya "ohh and you are calling me sarkin kishi ko?" Ya daga kafada "I wasn't complaining ai. Ina son kishin ki sosai. Yana kara kin confirming kina so na" nace "to yanzu su friends din naka babu abinda zaka shirya musu kenan?" Yace "kamar kin san da zu muka gama rigima. Sunce wai ban gayyace su daurin aure na ba ballantana in shirya musu reception and I told them ni ma ba'a gayyaceni daurin auren na wa ba. Haka suka zauna suka tsuye ni wai nayi musu karya nace kin mutu" na bude ido "what! Yaushe kace musu na mutu?" Yayi dariya "lokacin wancan daurin auren ne suka dame ni da tambayar ya akayi ba ke zan aura ba, and su ba su san irin heartbreak din da nake going through ba a lokacin, Ni kuma nace musu kin mutu" dariya nayi sosai sai ya tsaya yana kallona kawai yana murmushi. Sai kuma naga yayi sauri ya dauko wata leda a baya ya miko min "Har na kusa mantawa, I bought you chocolate slurry, irin wadda kike so" na dan bude ido kadan sannan na bude ledar na dauko dan karamin cup din ina kallon sa sannan na kalli Muhammad "a hana ni sha fa, kai fa kace min in ban daina sha ba zan zama katuwa" ya dan daga kafada "yau dai kadai. Daga yau ba zaki kara sha ba" na bude cup din na dauko dan karamin spoon din da yake makale a jikin cup din na diba na saka a bakina ina jin dadin narkakkiyar chocolate din da aka chakuda da madara kuma ba'a saka sugar ba, na kwantar da kaina a jikin motar tare da lumshe ido na memories din rayuwata da Muhammad yana dawomin kaina. Na bude ido naga idon sa yana kaina, na sake diba da spoon din na kuma sha sai yace "babu tavi ko?" Ban ce komai ba na dibo a spoon din na mika zuwa bakinsa. Mai makon ya sha sai ya kama hannu na ya dawo da shi baya ya mayar da spoon din cikin cup din sannan ya saka dogon dan yatsa na a cikin chocolate din ya dangwalo sannan ya kai bakin sa, na lumshe ido ina jin wani irin feeling na yadda yake yi wa finger din nawa a cikin bakinsa, nayi kokarin karbe wa amma yaki saki, sai ya sake mayar da shi ya kuma dangwalo wa ya sake mayarwa bakin sa, "hmmm" yace "chocolate din nan akwai dadi fa" ya sake kokarin mayar da yatsan nawa cikin cup din for the third time sai na janye cup din, "zaka shanye min ai'" na fada trying to make him stop, yace "rowa ko? To shikenan, ki rike taki chocolate din in rike tawa" ya fada tare da mayar da hannuna zuwa bakinsa. Sai da yabi fingers din daya bayan daya kamar wanda ya samu sweet din gaske, sannan ya juya hannuna ya manna min kiss a tsakiyar tafin hannun. Nayi saurin janye hannuna tare da boye shi a bayana trying to hide yadda yake saka ni nake ji. Ya sake cewa "rowa ko?" Na mika masa cup din gaba daya, "gashi na bar maka" yace "taki ce wannan ai, ki bani nawa kawai" na girgiza kai sai yace "okay to bana son wannan din, ki sha kayar ki kawaj" na dauki spoon din na cigaba da sha da sauri da sauri, ina son in rage wa zuciya ta bugawar da take yi. Sai da nayi nisa da sha sannan ya karbe cup din daga hannu na da hannun sa daya, daya hannun kuma ya kamo fuska ta ya juyo dani gare shi and unexpectedly ya hade bakin mu guri daya. Sanda ya sake ni babu sauran taste din chocolate a bakina, ya shanye tas, abinda ya rage min a bakin kawai taste din sa ne, wanda nake jin sa kamar ba'a iyakacin bakina kadai ya tsaya ba, kamar dukkan jijiyoyin jikina ya zagaya. Na bude idanuwa na da suka yi min nauyi na ssuke su a kansa, har lokacin fuskarsa tana kusa da tawa, idanun sa a cikin nawa, murmushi mai fadi akan fuskar ta sa yace "nima na sha tawa" sannan ya daga min gira yace "and mine is sweeter" na tura baki tare da saka hannu ina goge lips dina nace "kai kazami ne Allah kuwa" ya danyi dariya "kar ki damu, da sannu zan jaki zuwa class dina, watakila ma ki fini kwarewa" na murguda baki ina magana kasa kasa sannan na bude kofar motar na fita nace masa "kayi wa kanka, na fasa yin hirar da kaj" na rufe kofar sai kuma na sake budewa na dauki cup din chocolate dina nace "kuma ba zan bar maka chocolate dina ba" yayi murmushi "na sha tawa ai" har zan rufe kofar sai yace "hey Piya" na tsaya sai yace "I love you" na danyi murmushi ina jin har na huce nace "I love you too Baby". Na rufe masa kofar amma sai ya cigaba da zama a motar har na shiga cikin gida sannan ya tafi, Na danyi kokarin calming kaina down a compound amma shima da mutane dan haka na wuce cikin gida, ina shiga sai nayi sauri na wuce kitchen na wanke fuskata gabaki daya dan duk dankon chocolate take yi, sai kuma na zauna a kitchen din na cigaba da shan chocolate dina ina ta zabga murmushi ni kadai. Washegari da sassafe muka tashi muka shirya zamu tafi gurin gyaran gashi, na shiga yiwa Mommy sallama na tarar har lokacin rabon kaya take tayi, har zan fita sai ta kira ni "Safiyya, ni kuwa yaron nan bai yi miki maganar yadda yake ciki akan Safina ba?" Na danyi shiru ina kallon ta, trying so hard kar in nuna bacin rai na, sai kuma kawai na girgiza mata kai nace "a'a. Bai ce min komai ba" sai nayi sauri na fita daga dakin kar ta sake yi min wata maganar. Ni bana son jin duk wani abu daya shafi Safina da Muhammad, bai taba yi min maganar ta ba nima kuma ban taba tambayar sa ba. Duk wani hukunci da ya yanke ko zai yanke a kanta abinda ya shafe su ne bana son shiga ciki kuma bana son a shigar da ni. Muka je tare da Salima aka yi mana gyaran gashi, sannan aka yi min pedicure da manicure, aka kuma yi min teeth whitening sannan saloon din suka yi min massage for free a matsayin wedding gift din su. Daga nan muka dawo gida muka tarar mai kunshi har tazo, nan da nan na zauna aka fara rangada min jan lalle, bayan an gama akayi baki shima amma kadan as adon jan, sai ya fito yayi kyau sosai, har yamma bamu gama ba. Tun da rana kawayena na kano suka karaso, naji dadin zuwan su sosai dan akwai da yawa daga cikin su da mukayi shekaru rabon da muyi magana sai da bikin nan ya tashi na neme su kuma sai gasu sun zo. Ko dan nima na san I was quite popular a makaranta kuma da yawa kawayena suna sona. Lokacin yan gidan mu suna ta shirye- shiryen zuwa gidan su Muhammad wunin da aka gayyace su, sai a lokacin na lura ashe tare da garar da akayi min zasu tafi su kai musu, ni kuma ana gama min na shiga wanka nayi da special man wankan da mai gyaran jiki na ta bani, ina fitowa ta zo ta kuma turarani da turaren ta mai kamshi da kama dukkan sassan jiki, cikin sauri na saka rigar da na tanada for today's occasion sannan nay sallar magrib din da ake yi a lokacin sannan muka zauna zaman kwalliya, Sanda aka gama kwalliyar ni kaina zaman kallon kaina nayi a gaban madubi, lallai da gaske Muhammad yake da yace yana murna babu maza a bikin, dan ni kaina sai nayi kishin nunawa mazan da ba nawa ba wannan kwalliyar da kyan da nayi. Sai kuma naji ina son ya gani shi, ba wai a hoto ba, dan haka na dauki waya na kira shi "hey baby" duk yammatan gurin suka juyo suna kallona, nay musu fari da ido bayan naji ya amsa "kana ina?" Yace "ina gidan ki. Kin san ni yau nake tarewa. I am here busy arranging ny things" nace "zaka iya zuwa nan yanzu?" Ya danyi shiru "is everything okay?" Nace "komai lafiya. Nayi kwalliya ne nayi kyau, and I want you to see me" ya danyi murmushi mai sauti. "I won't miss this for a thing. Zan ajiye komai in taho. Sai in kaiki gurin taron. Ki ce suyi gaba zamu taho tare" nace "okay, sai kazo" na katse kiran ina kallon kawayena da suke bina da kallo, Nan da nan suka kama surutu "ba tun yau ba na fada, mijin Fiyya zai sha iyayi" "wannan soyayyar in da ace kina da kishiya ai sai ta hadiyi zuciya ta mutu" "ni kam zan so inje gidan ki watarana in ga yadda za'a ci wannan soyayya " "in dai mijin bai yi a hankali ba Safiyya will have him licking at her fingers" na sake juya idona nace "na nawa kuma? An wuce wanna gurin ai". Haka suna ji suna gani suka shiga motoci suka tafi nace ba zan tafi da su ba, Salima ma data makale sai ta bini wai ai ba'a barin amarya ita kadai haka na kora ta nace in dai bata tafi tare da su ba sai dai ta tafi ita kadai dan ba zata shiga motar mijina ba. Sauran mutanen gidan ma babu wanda bai yaba da kyan da nayi ba dan a lokacin suke dawowa daga event din gidan su Muhammad hannunsu cike da abin arziki. Suka yi ta daukan hotuna da ni har sai da Muhammad yace yazo sannan twins suka raka ni na fita wajensa. Bridal gown na saka fara sal, silky material a ciki mai karamin hannu sai kuma aka dora lacy material a sama shi kuma da dogon hannu, aka kuma yi dogon trail yana jan kasa sosai a baya na. A dai dai waist din rigar kuma anyi ago da flowers different colors an zagaye ni da su, sai kuma gashi na da aka gyara aka zubo min da shi ta side din kunnen hagu na sannan ya sauka har kafadar hagun ya kuma nannade a bayana, Anyi wa gashin ado da pins masu different colors kamar na flowers din jikin rigata. Sannan aka lullube gashin nawa da farin lacy veil, Takalmi da jakar hannu na duk sunyi matching da flowers din jikin rigata. Ya fito daga motar yana kallona baki a sake. Daga kallon kawai a san kwalliya ta biya kudin sabulu. [07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Sixty Six : Avenged Not completely edited 😁 I am tired as always. Tun daga fitar Aunty Hajjo sai na koma nayi shiru, tun kawayena suna tsokana ta har suka ga ina neman saka musu kuka sai suka rabu dani suka cigaba da hirarrakin su da shewa, suna ta labarin gida na da yadda komai na gidan yayi kyau ya kuma da ce da inda aka ajiye shi. A lokacin naji Farida tana tambayar "ku wai da gaske wadancan sababbin motocin da muka gani da bow a jiki gifts ne aka kawo mata?" Salima tace "eh fa. Kanin baban sane ya kawo musu ita da angon as wedding gift" Hasina tace "gaskiya mutanen nan suna da Naira, Kin san kuwa tsadar motar nan? Guda biyu just like that wai wedding gift?" Salima ta dan tabe baki tace "in dai kudi ne gidan su suka zo" sai muka hada ido na girgiza mata kaina, dan ni idan akwai abinda bana so shine bragging da arziki, in ka sani kawai ka sani in kuma ba ka sani ba bana bukatar ka sani sai dai in ta kama dole. Suna nan dai har suka yi sallar isha' i, kawayena da suka zo min from outside of Abuja duk gidan mu zasu koma su sake kwana sannan washegari su koma gidajen su. Around 8:30 sai ga kiran Muhammad, ban dauka ba sai na mika wa Salima, a zuciya ta ina tuna cewa tun safe rabon da inji muryar sa, da ta dauka sai naga tana murmushi tana kallona sannan tace "ba ita ba ce ba. Salima ce. Kunya take ji wai ba zata dauki wayar ba" sai kuma tayi dariya, sannan tace "okay, gamu nan zuwa" ta miko min tana murmushi "yace suna first floor, mu sauka mu same su". Muka tashi gabaki daya, suka sake gyara min laffaya ta suka rufe min koina har kafa ta, sannan suka kara min turare suka kama hannu na muka sauka zuwa falon da yake a hawa na biyu. Ni dai jana kawai suke har suka kaini kan kujera suka ajiye ni. Sai da na zauna sannan na fahimci a kusa da mutum aka zaunar da ni. Sai kuma naji muryar Ya Amen yana amsa gaisuwar da kawayena suke yi musu, tare da muryar wasu mazan amma kamar basu da yawa ba zasu fi su uku ko hudu ba. Daga nan kuma aka gabatar da addu'a aka shafa sannan Farida kawata tun primary school sarkin surutu ta fara zuba, har da yin speech akan wai sun bawa Muhammad amana ta, sai tazo ta kama hannuna ta dora akan nasa tana lissafa masa irin kyawawan halaye na, ta kara da cewa "amma fa sai kayi hakuri, akwai iyayi da taurin kai" ina jin Muhammad yana dariya. Sai kuma Usman abokin sa shima ya gode wa kawayena for hidimar da suka sha a lokacin bikin, ya kuma koda abokin na su da lissafa irin kyawawan halayen sa shima, sannan ya tabbatar wa da kawayena cewa abokin su zai rike amanar da suka bashi. Daga nan kuma sai aka fara cinikin fuskata, kawayena suka dan ware gefe daya suka yi meeting sannan suka yanki kudi mai tsoka suka fada, abokan ango suka fara jayayya, sun jima suna to and fro sannan suka daidaita akan price din da kawayen suka ki sauka daga kansa, daga nan abokai suka ce a bayar da account details din da za'a basu kudin, suka fadi account aka tura musu, sai da kudin ya shiga sannan naji kawayena sun hau shewa da hun murna, kudin da aka basu har yafi wanda suka tambaya da farko. Daga nan Salima tazo zata bude fuska ta ango ya hana, kiri kiri yace babu wanda zai ga fuska ta a cikin abokansa a ranar, ai kuwa nan rigima ta kaure tsakanin sa da su, suka yi masa gorin dama babu abinda ya shirya musu a bikin nasa, kuma fuskar amaryar ma yanzu ya hana su gani. Anan na jawo shi na rada masa cewa ya gaya musu ina gayyatar su cin taliyar amarya nan da kwana uku, amma da Muhammad ya tashi fada sai yace next week. Haka dai aka gama komai cikin raha da walwala sannan suka tashi suka yi min sallama suka tafi, duk wadda ta leka fuskata sai inji kamar in rike ta in hana ta tafiya amma ina ji ina gani suka tafi suka barni. Ni ko rakiyar ma banyi musu ba, Muhammad dai ya sauka ya raka abokansa ya kuma sake yiwa kawayena godiya, Sai da suka tafi sannan ya dawo. Har ya dawo ina zaune a inda ya barni. Naji shigowar sa amma sai naji shi shiru, ina nan dai zaune a inda ya barni. Ina jin a jiki na cewa kallo na yake yi, sai kuma naji yayi gyaran murya. "inzo in gani ni?" Ban yi magana ba sai naji shi ya karaso gaba na ya tsaya yace "ko nima sai na sayi fuskar amaryar ne?" Still bance komai ba sai ya durkusa a gaba na ina jin kamshin da yake tashi daga jikin sa, ya dan daga laffayar ya leka fuskata muka hada ido sai nayi sauri na rufe ido na, yayi murmushi mai sauti sannan ya daga laffayar ya bude ta gabakidaya ya sauke ta akan kafada ta yana karewa fuska ta kallo. Na daga idona muka hada ido yayi min murmushi "kinyi kyau sosai. Yau gabakidaya ban ganki ba" shima yayi kyau kwarai da gaske, yana sanye da riga da wando na yadi dark blue da akayi wa dinki mai kyau kuma suka fito da kyan fatarsa sosai. Hularsa ta zauna sosai a kansa kamar dan kan aka halicce ta. Amma sai na kasa ce masa yayi kyau. Sai naji bakina yayi min nauyi, na sake mayar da idona kasa sai ya zauna a kusa dani tare da rike hannuna yace "kinyi kuka k0? Ance min kinyi kuka a gurin Daddy ko?" Na gyada masa kai ban ce komai ba, ya saka yatsun sa guda biyu ya dago fuska ta ya juyo ta tana kallon sa, na sake daga ido na na saka a cikin nasa, sai yace "yanzu ma kamar kin sake wani kukan. Su Salima kika yiwa? o kukan Daddy da Mommyn ne har yanzu?" Ban amsa ba sai naji kamar zan sake yin wani kukan. Yayi ajiyar zuciya "thank you Piya. I cant thank you enough for your love and sacrifices. Ko barin gida da kika yi kika yarda kika taho nan zaki zauna da ni ni kadai is a very big sacrifice. Wannan abu ne da ba zan taba mantawa ba insha Allah. Na yi miki alkawarin in Allah ya yarda ba zaki yi nadamar zaba ta out of all the men in the world ba" a hankali nace "nima insha Allah ba zaka yi nadamar zaba ta out of all the women in this world ba" yayi murmushi. "Finally! Na sayi bakin". Ya mike tsaye ya mika min hannun sa "come, let's take a tour of our house" na saka hannu na a cikin nasa ya jani na mike tsaye, amma maimakon mu tafi sai naga ya fara kokarin kunce min laffayar jikina "akwai stairs, kar ki fad;" ya fada da yaga ina kokarin hana shi. Sai da ya warware ta sannan ya ajiye akan kujera yana kallona, naji kunya ta kama ni sosai, ban taba tsayawa a gaban sa haka babu mayafi ko hijab ba, gashi kuma dinkin jikina babu laifi ya fitar da shape din jiki na sosai. Shape din da ni kaina ina matukar ji da shi. Ganin kallon ya ki karewa ya saka na yi kokarin sake daukan laffaya ta duk kuwa da cewa ba iya daurawa zanyi ba, ya karbe daga hannu na yana dariya "'shikenan, na daina kallon ki" na harare shi, ashe ma ya na sane kenan. Ya zagaye waist dina da hannun sa ya jani zuwa jikinsa "you are just so beautiful, I still can't believe you are mine. Thank you for being mine" ban amsa masa ba dan harshena gabakidaya yayi nauyi, zuciyata tana bugawa da karfin da har nake jin ta cikin kunnuwana. Sai ya sauke fuskarsa akan kafadata sannan ya fara bin wuyana yana shanshanawa tare da goga min gashin sajensa. Na yi taku biyu baya da sauri wanda hakan ya sa jiki na ya rabu da nasa ina kallon sa, sai na ga ya fara dariya a hankali "kinga idonki kuwa Piya? Kamar an yi shaking rat a cikin kettle" na harare shi "kana sane ma kake tsokana ta wallahi. Allah Malam Muhammadu duk sai ma rama abubuwan da kake yi min kwanan nan" yace "ai haka nake so da ma n ai, so nake ki rama" na danyi murmushi ina kallon kasa sannan nace "wai yaushe table din yayi turning ne? Ni dai na san a da nice mai tsokanar ka kai kuma mai jin kunya amma yanzu kawai sai naga munyi chanjin positions" yayi ajjiyar zuciya tare e da yin taku biyu zuwa gaba na yace "a lot of things have happened, a lot of things have changed" na gyada kai na cikin amincewa sai ya jera dani yace "but nothing matters now tunda we are together ko?" Na zura hannuna ta cikin nasa da ya miko min ina kallon fuskar sa kamar yadda shima yake kallon tawa da murmushi sannan nace "let's take a look at our home". Gidan hawa biyu ne, ta kasa muka fara. Akwai katon falo a kasa, wanda shine kusan ya chine rabin ground floor din. Yana hade da dinning room mai girma shima, daga falon har dining din anyi sune kawai for occasions da za'a tara mutane da yawa. Bayan su kuma sai kananan faluka guda biyu iri daya at different sides of babban, daya nawa dayan na Muhammad, kowanne da two bedrooms da toilets a ciki, saboda baki, Daga nan kuma sai first floor, ana iya hawa ta falon Muhammad ana kuma iva hawa ta falo na. Shi kuma akwai madaidaicin falo wanda muka zauna dazu, akwai kitchen kato shima tare da store sai kuma madaidaicin dinning room a hade da falon. Daga nan kuma sai gym, wanda Muhammad ya cika da kayayyakin motsa jiki masu yawan da har sai da na tambaye shi idan gasar wrestling ta WWE yake so ya fara shiga. Daga nan kuma sai bangaren swimming pool, da muka shiga sai da na rike baki na cikin mamaki tare da jinjinawa Kamfanin su Ya Amen akan iya aikin su, gurin yayi kyau sosai kuma gabaki daya a zagaye yake da glass din da kai da kake ciki zaka ke ganin kowa a waje amma babu wanda zai iya hango ka daga waje. Katon swimming fool ne a tsakiyar gurin blue tiles din da aka shafe jikinsa da su suna chanja color zuwa different shades of blue saboda fitulun da aka saka musu. Akwai grin yin shower da kuma changing room a cikin gurin sai kuma kujeru guda biyar. Instead of tiles, grass carpet ne a lullube a kasan gurin. Daga yadda na nuna Muhammad ya fahimci bayan kitchen nan ne favorite spot dina a gidan, Daga nan kuma sai sama ta biyu. Da akwai stairs daga gym da zasu kai ka saman akwai kuma wasu daga falo, A sama ta biyun kuma bedrooms ne kawai. Bedroom dina da na Muhammad iri daya ne exactly. Girman da komai daya ne. Ni ba bedroom din ko kayan cikin sa na fi so ba na fi son closet din. Daga bedroom din zaka shiga kofa, a hannun dama akwai toilet, a hannun hagu kuma closet. Zan iya cewa kusan girman su daya da bedrooms din dan ni nawa bayan lockers din da aka zagaye bangon su da su har kujera na saka a tsakiyar closet din, irin katuwar kujerar nan wacce ake iva mayar wa gado, a gaban kujerar kuma katon mirror ne, both sides of mirror din kuma kananan drawers ne da zaka iya ajjyar kayan kwalliya. Daga hannun daman ka in ka shigo closet din kuma study table aka saka, anyi masa dukkan tsare tsaren da zan iya yin aikin office dina ko karatu ko whatever nake bukata a gurin, lokokin gurin takardun aiki da duk was littattafai zan saka. Hannun hagun kofar kuma gurin yin sallar ne, an shimfida praying mat sannan anyi provision for gurin ajiye Alqur'ani a lokacin karanta shi, lokokin wajen kuma zan zuba littattafan addini ne a ciki. Zan iya shiga cikin closet dina in wuni ba tare da na bukaci fitowa ba, sai dai a kai min abinci, Komai na bedroom dina fari ne tas, sai da Aunty Hajjo ta dage sannan na bari aka sirka farin kadan da light ash. Daga dakunan mu kuma sai dakunan da akayi su a matsayin extra bedrooms guda biyu iri daya, ni kuma a raina sai na lissafa su a matsayin dakunan yara idan Allah ya bamu nan gaba. Sai da muka gama da nawa muka yi hanyar nasa sai ya tare kofa yana shafa kai, na tsaya ina kallon sa nace "ba ka da gaskiya" ya danyi murmushi "it is kind of messy" na harere shi "kazanta ko?" Ya daga kafada "ba laifi na bane ba ai. Ke kika hana ni zama in gyara jiya kuma sanda na dawo na gaji. Yau kuma tun safe Mama bata barni na zauna ba ina ta zirga zirga" na dan sunkuyar da kaina kasa nace "anan ka kwana?" Ya danyi murmushi "a ina to zan kwana idan ba'a gida na ba?" Ban ja maganar ba dan bana son yin maganar sai na cire hannun da ya tare kofar nace "saí naga abinda kayi a dakin" na shige da sauri kafin ya sake tare ni. Ina shiga dakin na sa sai naji kamar ya kwace wa kitchen matsayi a waje na. Maimakon nawa da yayi haske saboda white color da akayi using, shi nashi royal blue ne da sirkin golden. Wannan ya sa dakin yayi duhu and it looks very cozy. Na lumshe ido na ina shakar kamshin sa da dakin yake yi, sai ya zagayo ta bayana ya rungume ni ta baya "to ya? Bulala nawa za'a yi min ta bata daki da nayi ban gyara ba?" Babu wani hargitsewa da dakin yayi, dagon dai ba'a gyare yake ba beddings din duk a cukurkude, sai kayan sa kamar set biyu a ajiye akan side drawers din gefen gadon daga gani cire su yayi bai adana ba, ga kuma takalma suma kafa biyu a watse a tsakar dakin. Daga can kasan window kuma akwatinan kayansa ne ko shigar da su closet bai yi ba ballantana ya jera. Nayi kokarin juyo wa in kalle shi amma sai ya kara matse ni da jikinsa shinshinar bayan kunne na "'hmmm, kamshin ki dadi" ya saka hannu ya ture dankwalin kaina sannan ya zare ribbom din dana nannade gashi na dashi, gashin ya zubo har saman kafadu na sai kuma ya saka fuskarsa a cikin gashin tare da kara sauke wata ajjiyar zuciyar,. Nayi kokarin bambare hannunsa da ya zagaye ciki na shi amma sai ya kara matse ni a jikinsa yana shafa dogon gashina da dayan hannun na sa, nace "kana wayencewa ne kawai dan kana jin kunyar messiness of your room" ya danyi dariya kadan, "zan gyara, amma bara in gama wannan gyaran tukunna" na juyo da sauri amma bai barni na bar jikinsa ba sai ya sake hade jikin mu muna fuskantar juna idanun sa akan lips dina, na dan ja fuskata baya na kara distance a tsakanin lips din mu "na ga dakin ka, yayi kyau. Now let's go '" ya danyi dariya a cikin kirjinsa yana biyo fuskata da tashi "let's go where? Ai nan ne final destination din. Ko baki san nan ne turakar mijin ki ba" nayi shiru ban ce komai ba ina cigaba da kokarin hana shi hade bakin mu, ina jin yayan hanjina suna karkarwa. Ya cigaba da magana, ina jin motsin lips dinsa akan nawa "kin san me akeyi a turaka?" Ban amsa ba dan banajin zan iya amsawar, numfashin sa kawai nake shaka. "in gaya miki? In nuna miki?" Na girgiza kaina da sauri "bana son gani. Bana son ji. Ni dakina zan tafi" yace "hmmm" tare da kissing hancina da kuma haba ta, cikin dauriya nace masa "kai ma hmmm" sai yayi dariya, "ba kin ce kina son sanin ma'anar hmmm dina ba?" Nace "bana so, na yafe, Ka rike ma'anar abinka" dariya ya danyi tare da goga min sajensa a gefen fuskata "ko ba kya son sani yau sai na sanar da ke" ya fada yana sake dawo da bakinsa kusa da nawa. Na matse lips dina na shigar da su cikin bakina sai ya sake yin dariya tare da mintsini na a cheek dina, na dan yi kara "har da mugunta kuma? Daddy ya .... Ban gama ba ya mayar da maganar tawa ciki ta hanyar hade bakin mu. Sai da yayi mai isar sa sannan ya janye bakinsa, ya tsaya yana kallona idanuwana a lumshe, sai ya mayar da bakin sa kunne na yace min "I have got a favorite thing to do yanzu. Kissing you is now my favorite thing to do" na bude ido na ina kallon sa sai ya kama hannuna "come, na siyo miki kaji, kar ki ce nayi miki rowa". Ya jani ya zaunar da ni akan hargitsatstsen gadon sa, sannan yace "ina zuwa, minti biyu, kar fa ki gudu" duk da halin da zuciya ta take ciki sai da na danyi dariya. Ya fita da sauri ni kuma na cigaba da zama ina karanto dukkan adduoin da na ke ganin zasu vani kwarin guiwar fuskantar mijina. Kullum in ana bayanin toro in aka ce mutum yana jin kayan cikin sa suna rawa bana iya gane wa, amma yanzu na gane, yanzu nima nawan rawa suke yi sosai, hatta hakora na karkarwa suke yi, Babu abinda yake yawo a kaina sai azabar da Mukhtar ya ganar da ni, sai irin tsoron da naji a lokacin da yake gana min azabar. Na sani cewa Muhammad ba Mukhtar ba ne ba, na kuma yarda cewa ba zai cutar da ni ba. Amma kuma na kasa cire tsoron daga zuciyata. Ya dawo hannayen sa dauke da ledoji manya guda uku, ya ajiye su a gefe na yana kallon dakin yace "gaskiya naji kunya da yawa" sai ya sunkuyo kawai naji ya daga na chak, na bude ido da sauri ina kallon sa sai naga ya ajiye ni akan kujera sannan ya juya ya fara gyara gadon, ina kallon sa har da dauko turare ya fesa a beddings din, gyaran na shi dai daga gani ba iyawa yayi sosai ba irin yadda nake so, amma dai ya gyara. Sai kuma ya kwashe tarkashen kayan sa ya shiga da su ciki, ya fito yana sake kallon dakin sannan ya kalle ni yace "yayi ko?" Ban amsa masa ba sai ya karaso gaba na yace "sallah ko kaza?", A hankali nace "ni sallah zanyi. Ni ba zan ci kaza ba, Nina koshi" ya danyi dariya "kwadayayyiya, ranar nan ma haka kika ce ai, sai gashi har kin fi ni ci" na dan harare shi kadan. Sai ya wuce zuwa toilet dinsa yayi alwala, ni ma yana fitowa na tashi na shiga, na jima a cikin toilet din ina kokarin calming kaina down sannan nayi alwalar nima na fito. Na tarar da shi ya shinfida mana wani karamin carpet akan carpet din da yake dakin already, naji kamshin dakin ya chanja kamar ya kara wani turaren na daban mai dadin kamshi, "bani da hijab" na ce masa, "bara inje daki in dauko" ya girgiza min hannun sa "uhm uhm. Ki zauna anan inje in dauko miki" na bude hannu na, "to ai baka san inda yake ba" da kyar ya yarda muka tafi tare, ban sani ba ko tunani yake yi zan gudu idan na tafi ni kadai? Na dauko hijab dina na hada da kayan bacci na da sauran abubuwan da nake bukata idan zanyi shirin kwanciya. Kamar wadda zanyi hijira zuwa wani garin. Muka koma dakin nasa na ajiye kayan da na debo sannan na saka hijab dina muka tayar da Sallah. Bayan mun idar shi yayi mana adduoin masu tsaho, nayi mamakin yadda ya juya bakinsa yana jero mana adduoi cikin karshen larabci, sai naji kamar yaren sa ne, muka shafa sai ya tambaye ni idan ina da wata addu'a da zanyi mana sai na daga hannu na a zuciya ta na roki Allah ya yaye min wannan tsoron da nake ji sannan na shafa, ya shafa shima sannan ya yambaye ni "mai kika roka mana?" Na girgiza kaina "shirri ne" ya bude ido sirri? A tsakanin mu da ma akwai sauran secret?" Na sunkuyar da kaina ban ce komai ba. Ina jin sa yana cigaba da kallo na sai na dago kaina na kalle shi cikin ido nace "Yaya Muhammad" bai amsa ma amma gabakidaya attention dinsa yana kaina, a hankali cikin karyewar murya nace "tsoro nake ji, I am scared Yaya Muhammad" bai ce min komai ba sai naga ya sunkuyar da kansa yana kallon kan cinyata, nima na kalli inda yake kalla sai na ga hannayena da suke kan chinyar sun karkarwa kamar wadda take jin tsananin sanyi, nayi sauri na rike su da junansu sai ya matso ya dora nasa hannayen akan nawa ya rike gam har sai da suka daina karkarwar sannan yace "I know. Na san kina jin tsoro Safiyya, sai dai kuma bayan haka na san wani abu daban, na san kina sona kamar yadda nima nake son ki" ya gara zaman sa sosai sannan ya cigaba "kin san wani abu? ranar da kika je office dina a MD kika gaya min cewar kina da aure, I was devastated a lokacin, maybe tashin hankalin da na shiga shi ya hana ni ganin gaskiya, amma bayan na koma gida, bayan na nutsu nayi tunani sai na tuno da fuskar ki a lokacin da kike yi min maganar, na kuma tuno da yadda kika furta kalaman, sai kawai naji na fahimci wani abu, na fahimci kina so na sosai, wannan son kuma shine abinda ya bani hope, shi ya rike ni ya hana ni hakura da ke inyi moving on, ya hana ni giving up. Tun daga lokacin kuma har zuwa yanzu soyayyar ki ita ce take jagoranta ta a dukkan decision dina, yanzu ma kuma ita ce hope dina. You have fear, Yes, but you also have love". Ya mike tsaye tare da mikar da ni tsaye nima sannan ya zaunar da ni a bakin gado sai ya tafi gurin ledojin da ya shigo da su ya dauko wata karama ya dawo kusa da ni ya zauna ya bude ta ya dauki wasu boxes guda biyu kanana tare da wasu takardu, ya ajiye takardun sannan ya bude box din farko ya nuna min "look at this beauty" na kalli abinda yake ciki, a take na bude baki, ya danyu dariya yana jin dadain yabawa abinsa da nayi. Zo be ne na diamond, anyi mass rings din sirara guda uku amma saman su an hade shi da dunkulallen diamond mai shape din heart. Ya fito da shi sannan ya kama hannuna ya saka min, yayi dai dai a danyatsa na kamar an gwada, kamar ya san me nake tunani sai yace "na karbi measurement dinki ne a wajen matar da ta hada lefe. Do you like it?" Na sauri nace "like it? I love it Baby. Thank you" na fada tare da daga shi ina kallon sa sosai, a cikin heart din anyi design din rose flower, petals dinta different colors kuma na lura kamar colours din nasu yana chanja shade idan aka haska shi, yayi murmushi ya sake kama hannun nawa yana shafa yatsun yana kallon ring din sannan ya kai shi bakinsa ya sumbata yace "I may not have a gold company and all the rest, but I do have love and I am today giving you all of my heart together with all of my love, as far as love between couple is concern. I want to share my parents, my siblings and all of my family with you. I want to share my life with you. And I promise you that I will work hard to give you all that you deserve. And I promise you, insha Allah, that you will never shade sad tears again, sai dai in abinda yafi karfina, and ko da yafi karfin nawa ma, I promise you that we will cry together, wipe away each other's tears, and pick up each other. We will walk through the journey of this life together. You will never be alone again", Na fara sheshshekar kuka ina kallon sa "Muhammad……Yaya Muhammad....... have been through a lot a rayuwata, zan iya cewa tun kafin a san za'a haife ni rayuwa ta take dabaibaye da tragedies iri iri. At a point na dauka cewa ny family is cursed. Amma yanzu.... Yanzu da nake ganin ka a gaba na..... Sai na fahimci cewa kai ne sakamakon da Allah yayi min a duniya for all that I went through. Kai ne light din da ta jira ni at the end of the tunnel. Yanzu na fahimci duk abinda ya same ni Allah yana jaraba nine dan yaga idan na cancanci ya bani kai. Thank you. Thank you for loving me. I love you so much Baby na". Na fada kirjin sa ina cigaba da kuka na. Sai da ya bar ni na danyi kadan sannan ya dago ni yana kallon fuskata yace "next year by now, babyn mu yana kuka ke ma kina kuka. Da ana bayar da sarautar kuka da na nada ki" na harare shi tare da magana kasa kasa "ni sai na yi kuka na wallahi",. Ya kalli daya box din da take ajiye yace "baki saka min nawa ring din ba fa" na dauka da sauri na bude ina kallon nashi zoben, irin nawa be sak sai dal shi nashi anyi da azurfa ne ba diamond ba, Sannan instead of rings duda uku nashi mai kauri ne guda daya, kuma rose din cikin nashi bata colours kamar tawa. Na kama hannunsa na hagu na cire zoben da yake jikin danyatsansa na hudu na saka masa zoben, yayi mass kyau sosai ya kara haska hannun. Ya miko min hannun tare da hade rai "and now you kiss it". Na makale kafada "kai komai kiss komai kiss" yace "au haka kika ce? To wallahi sai kinyi" ya taso kaina kamar zai hau jiki na sai na yi sauri na kama hannun nayi kissing na mayar masa da kayan sa, yace "Allah ya taimake ki yarinya". Ya mike tsaye "yanzu kuma saura in baki kaza ki ci." Na makale kafada "ni fa na gaya maka ba zan ci ba" ya wani table ya kawo gaba na "to shikenan, ba zaki ci ba ni zan baki a baki" ya dauko another leda ya bude, kaji ne a ciki ba zan iya cewa ga adadin su ba saboda anyi pieces da su, ashe har da guzurin plate din sa a cikin ledar, ya zuba a cikin plate din sannan ya dora akan table din sau kuma ya fito da wani drink da ban taba gain irinsa ba ya zuba a cup ya ajiye a kusa da plate din sai kuma ya bude daya ledar, na lura fruits ne a ciki, sai yace "na manta ban dauko wuka ba" nace masa "ni fa ba ci zanyi ba" bai nuna yaji abinda nace ba sai ya durkusa a gaba na ya dauki tsokar naman guda daya ya kawo baki na "bude. Bude mana" na bude a hankali ya tura min a ciki "sai kinci naman nan yau ko dura zanyi miki. Kin san dadin sa kuwa? To wannan yafi na ranar nan dadi" naji dadin masa kuwa, amma ni yanzu ba ta nama nake yi ba. Kalamansa su sassauta min toro na amma fa yana nan babu inda yaje, sannan kuma a cikin kalaman na sa banji inda ya am bata cewa ba zaiyi ba, sai ma zancen Baby da ya yi min. Haka ya ringa cusa min naman nan, sannan ya dauko drink din ya kawo bakina "sha wannan. I bet duk yawon kasashen ki baki taba shan wannan ba" na kurba, yayi dadi sosai, na karba na kara sha yace "kinji da dadi ko?" Sai na gyada kai na zuba wani na mika masa. "'yayi dadi. Na gode. Na koshi. Kai ma ka sha" ya karba ya shanye sannan ya ajiye cup din tare da mike wa. yace "yau yaki za'a yi in gaya miki, between your fear and my love. Zamu ga wanda zai ci nasara. Ni kuma na san nine da nasara, Tunda na san love is the greatest weapon of all. Da mana jima ina share hanya, yanzu filin yaki kawai zan shiga ko a mutu ko a yi raj" yadda yayi maganar sai ya bani dariya, amma kuma ban dara din ba dan babu dariya a tare da ni. A dai dai lokacin ne kuma abin ya faru. Ina zaune akan gado ina facing kofar shigowa, shi kuma yana tsaye a gaba na yana kallona ya juya wa kofa baya. Idona yana sunkuye a kasa, amma duk da haka sai na ga kamar kofa ta motsa duk kuwa da cewa babu kara. Nayi sauri na dago kaina and I saw him, a tsaye a bakin kofar, muna hada ido ya karasa shigowa ciki da sauri sannan ya ja kofar ya rufe ya murda key din sannan ya zare key din ya saka a aljihu. Mukhtar. Kusan abinda ya faru ya faru ne in seconds, a take na kwalla kara muryata da fuskata cike da toro, dukkan tsoron da nake kokarin dannewa ya ninninka kansa sau babu adadi. Muhammad ya juya da sauri saboda ganin inda nake kallo da kuma razananniyar karar da nayi. Cikin bazata Mukhtar ya damki wuyansa sannan ya hankada shi da karfi ya buga shi a jikin bangon dakin, Kansa ya bugu a jikin bangon, dama gashi bai jima da jin ciwo a ka ba, ya dafe kan yana kokarin regaining kansa, wannan ya bawa Mukhtar damar binsa ya kuma damkar makogwaronsa tare da matse shi a jikin bango da dukkan karfin sa. Muhammad yana da girma, dai dai girman da namiji matashi mai irin shekarunsa ya kamata ya samu, Mukhtar ba sa'an sa bane ba, sannan kuma Mukhtar kato ne, tun yana yaro dama Mukhtar ba karami bane ba dan haka yanzu za'a iya kiran sa da katon mutum. Na sake kurma wani hun tare da yin tsalle na tsallake table din gaba na nayi kan Mukhtar ina dukan sa da dukkan karfin da Allah ya bani. "Ka sake shi.…. Ka sake shi ....." Na cigaba da ihun a yayin da Muhammad ya samu ya banbare hannun Mukhtar da kyar daga makogwaronsa. "Run........" Yace min "ki shiga toilet ki rufe kofa" ya kara fada a lokacin da Mukhtar ya murde masa hannun sa zuwa bayan sa sannan ya sake hada shi da jikin bangon kansa yana sake buguwa". Tsoron Mukhtar da nake ji ya rinjaye ni da farko, na ruga toilet da gudu kamar yadda Muhammad yace min amma kuma sai soyayyar Muhammad ta hana ni shiga toilet din, In na shiga na tsira dan na kofofin gidan suna da kyan da Mukhtar ba zai iya balla su ba, Amma kuma Muhammad fa? Zai iya yi masa komai musamman idan ya kasa samu na, sai na juyo a guje kamar yadda na tafi a gujen amma sai na fara bude window nayi ihun neman taimako sannan na dawo na fara daukan duk abinda zan iya dukan Mukhtar da shi ina kwada masa. Dakin babu wani tarkace a ciki, dan haka sam babu wani abu da zan kira makami. Naji ina missing wukar da take kasan gado na a gidan Daddy, na kuma jinjina hikimar Annabi da ya shawarce mu mu ringa ajiye makami a dakunan mu. "Run nace miki. Take my phone and lock yourself in the toilet. Then call someone" na girgiza kai ina jan hannun Mukhtar da dukkan karfina "gurina na kazo. a sake shi. Don't hurt him. Ni kai min duk abinda zaka yi min ka rabu da shi" na fada ina hada masa da duka da yakushi da duk abinda zan iya, na lura a jike yake da gumi, na lura har wan wari yake yi. Ya saka hannu daya ya ture ni na fadi kasa, Muhammad ya zaburo "don't touch her!" Ya fada a zuciye, Mukhtar ya sake mayar da shi ya buga a jikin bango "or what? In na taba tan me zakayi? Mama's boy. In na taba tan babu abinda zaka iya sai dai ka ruga gida da gudu kana kuka kaje ka fada wa maman ka. Stupid, Shashasha, Ban taba ganin sakarai irin ka ba. Duk shekarun da kuke tare, duk kyawun nan na ta, na dauka you already had her ashe kai sakarai ne, wata kila ma baka iya ba. Maybe kana jira sai an koya maka ne a gida" Muhammad yace "say whatever you want to say, maganar dai guda daya ce, ba ta son ka ni take so, shine kuma abinda yake damunka. Shine abinda duk ya jawo maka halin da kake ciki" ran Mukhtar ya sake baci "karya kake yi, tana so na. Ni ta zaba. Da kanta ta zabe ni tace ni zata aura. laifi ne kawai nayi mata. Fushi ne kawai take yi. She is mine, mine, mine, ni kadai. And I am here to take her. Zan tafi da ita in bata hakuri mu cigaba da zaman mu" "delusional" shine abinda naji Muhammad ya fada masa. Ya sake shi ya matsa baya da sauri, daga gani kasan ba'a cikin cikakken hankalin sa yake ba. Muhammad ya durkusa yana mayar da numfashi. Sai kuma Mukhtar ya juyo yana kallona da irin kallon da na saba gani a idonsa sanda ina gidan sa, kallon sha'awa "or maybe I should have her here" na mike tsaye da sauri, ya juya yana kallon Muhammad yace "I will have her here a gaban ka inga abinda zaka yi a kai". Bacin ran da na gani a fuskar Muhammad ban taba gain irin sa ba a duniya, ban taba tunanin yana da irin sa ba. A fusace yayo kan Mukhtar, Mukhtar ya rike hannun da ya kai masa duka da shi ya hana shi zuwa jikin sa, nan take suka cigaba da gumurzu. Na dauki wayar Muhammad a kan table kuma sai na rasa wa zan kira, wa zan tayarwa da hankali. Na sake lekawa da taga na cigaba da ihun neman taimako, na tabbatar security na suna waje, na kuma tabbatar sun ji ni, amma tashin hankali na daya shine tun sanda muka sauka kasa da niyyar kallon gida Muhammad ya rufe kofa, duk kuma inda muka shiga muka fito sai ya rufe kofa. Dan haka kofa nawa zasu bude kafin su shigo inda muke. Na kuma tabbatar sun kira duk wanda ya kamata su kira, maybe sun kira police ma already. Na tuna bindigar da suka bani, tana can dakina a cikin safe din gwala-gwalai na na wajen Ammie, Amma kuma sai naga Muhammad ya fara bani mamaki a fadan nasu, a da in za'a ce min za'a yi fada tsakanin Muhammad da Mukhtar ba zan dauka cewa Muhammad zai lasting minti biyu a hannun Mukhtar ba, amma sai naga yana neman ya gagare shi. Na fahimci Mukhtar kokari yake yi ya hada hannayen Muhammad ya rike da hannu daya dan ya samu damar shake mass wuya da daya hannun, so yake ya sumar da shi, may be a lissafinsa sai ya dauke ni ya gudu da ni. Amma Muhammad ya hana shi wannan damar. Daga wancan bangon su koma wannan bangon har suka fadi a kasa, Mukhtar yana saman Muhammad yana ta kokarin kama makogwaronsa, a lokacin naji alamar an shigo cikin gidan, sai dai ban san a wanne floor suke ba, na ga wani frame a cikin bango na hau kan table na ciro shi na buga wa Mukhtar a ka amma ko gezau bai yi ba. A lokacin na lura da abinda Muhammad yake yi, kafafuwan sa da suke free yayi amfani da su ya bude kafafuwan Mukhtar, sannan cikin dabara da karfin da na kara fahimtar yanzu yana da shi ya dake shi da karfi da guiwar sa a tsakanin kafafuwan sa. Mukhtar ya sake shi sannan yayi baya yana rike inda ya dake shi din, cikin zafin nama Muhammad ya tashi ya kara masa wani kyakyawan dukan a gurin again. Mukhtar yayi kara ya fadi tare da hade kafafuwan sa a waje daya cikin nuna ciwon dukan da yaji, amma Muhammad sai ya saka kafa ya sake bude kafafun ya kuma take gurin da karfi da takalmin kafarsa, Mukhtar ya saki karar azaba, kamar an cire masa dukkan karfin jikin sa, Muhammad ya sake duka, again and again and again. Har tsalle yake yi sannan ya taka gurin ya murje ya kuma takawa, ban taba ganin ran Muhammad a bace irin haka ba kuma bana fatan sake gani har abada. Jinin da naga yana bin wandon Mukhtar ne ya saka na fara kokarin rike Muhammad amma yaki rikuwa, a dai dai lokacin da aka fara kokarin bude kofar dakin da muke ciki ne na ga ya bar shi, na dauka da gaske barin na sa yayi, sai kawai na ga yaje a kinkimo wata flower vase da take kofar toilet dinsa, ya zo ya daga ta ya sakar wa Mukhtar ita a tsakanin kafafuwan sa, Ta daki gurin sannan ta tarwatse. A dai- dai lokacin da security din suka shigo dakin da muke hannayen su rike da bindigogi. Nayi sauri na rungume Muhammad, ina jin yadda jikinsa yake karkarwa, ina jin yadda zuciyar sa take bugawa, ina jin yadda numfashin sa yake fita sama sama. Chief security din ya kalli Mukhtar da yake yashe a kasa yana fitar da numfashi sama sama, ya saka kafa ya shure shi dan ya tabbatar babu sauran fada a tare da shi sannan Chief security din ya tambaye ni "are you okay?" na gyada masa kai kawai. Su biyu suka kama hannayen Mukhtar suka ja shi a kasa suka fita da shi. Na bishi da kallo, remembering everything that happened, and I thought "What a glorious God I have". Ni na tabbatar ta Mukhtar ta kare, abin nan dai ba zai kuma amfani da shi ba har abada, ba a kaina ba, ba'a kan kowa ba. Na kuma san Muhammad ya daki banza, ko shari'a za'a yi Mukhtar ne a kasa, sannan knowing irin gatan Muhammad, bana jin ma za'a yi shari'ar. Hukuncin da addinin musulunci ya tanada for rape, shine Mukhtar ya kawo kansa har gida Muhammad ya yanke masa. Na kara rungume Muhammad, jiki na gabaki daya yana karkarwa. A hankali ya fara sauke ajjiyar zuciya sannan ya dago fuskata daga kirjinsa yana kallo na yana shafa fuskar yace "Hey. It is okay. It is over. He will never touch you again. He will never touch any woman again". Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Sixty Eight: Detached Not Edited Him👳🏻‍♀️ Washegari ma bacci suka yi sosai da safe, basu tashi ba sai around 12, ita ta fara tashi ta gudu dakin ta ta barshi, rashin jin duminta ya saka shi tashi shima. Yau ma kamar jiya Mama ta aiko musu da abinci sannan Esther ma da take gidan tayi, suna vin breakfast suka sake dawowa sama. A wanna ranar sunyi abubuwa da dama, most of which includes exploring their bodies, aside that sunyi arranging and rearranging dakin sa. Daga cewa tazo ta taya shi shirya kayan sa a closet dinsa sai ta tsiri rearranging bedroom din nasa ma gabaki daya bayan sun gama da closet din, da kyar ya samu ta bar masa gadon sa a inda yake shima dan ya ce mata ba zai iya kunche shi bane ba, but kujerun sai da ta saka shi chanja musu guri daga inda yake so zuwa inda take so duk kuwa da cewa dakin sane kuma kujerun sa amma haka ya juya su da kansa zuwa ra'ayin ta, bayan ta zama satisfied with the arrangement kuma ta matsa masa lallai shima sai ya amince cewa kujerun sunfi dacewa a inda ta mayar da su, da yaki fada sai tayi fushi, dole ya fadi abinda take so din sannan kuma ya bata hakuri for not saying it a sanda takeso. Shi dama ya san ya debo wa kansa rigima with auren Safiyya but he was so looking forward to it and he knows yana da hanyar controlling dinta a gurin da take bukatar control din, but for other petty things like this, zai barta to have it her ways. Shima kuma sai ya taya ta gyaran tata closet din, a nan ya sha iyayi har sai da ya gode Allah, hatta folding kayan da ba'a dinka ba sai da ta nuna masa yadda zaivi, ballantana wadanda suke dinkakku, daga baya sai ya ce zai yi hanging abayas da English wears tunda su ba folding dinsu za'ayi ba, amma nan ma sai da ta zo ta nuna masa yadda ake saka veil din kowacce abaya tare da abayar a jikin hanger dinta, haka da suka zo kan takalma da jakankuna suma, wai kowanne takalmi sai an nemo jakarsa an ajiye su adjacent to each other, a shirya kayan kwalliya ne gayyar ta watse, suka bar aikin kuma suka koma wasa wai shine makeup artist ita kuma client dinsa, haka ta zauna akan kujera yayi ta shafa mata abubuwa a fuska, wani abin ma duk da ya karanta description dinsa amma baya gane amfaninsa dan haka ba'a gurin da ya kamata a saka shi ya saka shi ba, a karshe sai gata ta fito kamar mahaukaciya sabon kamu, ya saka ta a gaba ya ringa kyalkyala mata dariya, wannan dariyar da yayi ce ta saka tace wallahi sai ta rama, ya yi kokarin gudu ta kamo shi ta dawo da shi ta zaunar da shi shima ta tsara masa kyalliya tas a fuskarsa sannan ta rama dariyar da yayi mata. Haka suka zauna suna kallon junansu suna tuntsira dariya, a karshe dai suka gaji dan kansu suka zauna suka goge wa kansu kwalliyar. Da rana ma Mama ta aiko musu da abinci. Yau ma kamar jiya, sun fita sun je duba Daddy bayan sallar magrib kamar yadda yayi mata alkawari, bayan sun gaishe da Daddyn sai ta shiga ta gaishe da Mommy tunda ta lura yan kano sun koma. Da sauri ta shiga ta fito saboda yana jiranta, suka tafi. Wasa wasa sai gashi wankin hula yana neman ya kai Muhammad dare, love din da yake ikrarin zaiyi fighting fear amma sai ya kasa, sai dai kuma ya fahimci cewa fadan was no longer between love and fear but between love and love. Tana jin toro sosai, shi kuma yana sonta sosai, dan haka ya kasa takura mata dan yana jin tausayin ta sosai. She would let him kiss her, touch her, carry her and fly away with her in to the sky, zasu yi souring har su tarar da cloud eleven but she wouldn't let him do the do, da zarar ta ga ya dauki wannan hanyar zata rikice ta zare jikinta daga nasa jiki yana karkarwa, idanu suna fitar da hawaye, a haka dole zai hakura, and then she would ask him to hug her and sleep with her wai toro take ji. "Baby I'm scared" haka ta kan fada cikin shagwabar ta da take kara rikita masa tunani. A haka kwanaki uku na farkon auren su suka zo masa, Duk da cewa abubuwa ba su zo masa a yadda ya tsara su ba but he wouldn't change a thing idan da ace za'a bashi damar chanjawar, har zuwan Mukhtar ma ba zai chanja ba, dan zuwan na shi ya bashi damar hadiye wani abu da ya tsaya masa a makogwaronsa tun sanda Safiyya ta bashi labarin abinda Mukhtar din yayi mata, Abinda ya fahimta da ita shine ba wai bata son abin bane ba, ya fahimci tana so, just that wancan memory yana sakata tana jin toro sosai, maybe tana gain kamar abinda ta ji a wancan karon shi zata sake ji a wannan karon, duk kuwa da cewa a zuciyarta ta san ba haka bane ba amma kwakwalwarta taki karbar gaskiya, the trauma is still with her and she panics at the slightest thought of it. Wannan ya kara masa jin tausayinta da kuma lallabata. Washegari, maana ranar da suka kwana na uku together, bayan sun yi sallar asuba sai suka koma bacci kamar yadda suka saba yi kullum, ya rungume ta a jikinsa ya lullube su nan take bacci mai nauyi ya dauke su, sun jima suna yin baccin sannan karar wayarsa ta tashe shi, cikin bacci ya jawo wayar and sunan da ya gani a jikin screen din ya bata masa mood dinsa, ya katse kiran sannan ya saka wayar a silent, ya koma da niyyar cigaba da baccin sa amma sai yaji baccin yaki zuwa, reality din situation dinsa yana lullube shi, kafin ya gama analyzing situation din nasa yaji wayar Safiyya ta dauki kara itama, kasancewar tana bangaren ta sai ta riga shi dauka and cikin bacci ba tare da ta duba sunan wanda ya kira ta ba ta amsa ta saka a kunnen ta tare da cewa "hello" cikin muryar bacci, kusancin da suke da juna ya saka yaji muryar da kuma abinda ya fito daga cikin wayar ta ta, muryar Safina "na kira wayar sa bai dauka ba, na san kuna tare, ki gaya masa ko ince ki tuna masa cewa yau kwanan ku uku tare, hakan yana nufin yau kwana na ne tun da dai ke bazawara ce ba budurwa ba......" ya saka hannu ya zare wayar da ga kunnen ta sannan ya katse kiran ya ajiye tare da rintse idonsa yana jin zafin maganar kamar shi aka gayawa, sai kuma ya sake juyawa wajen Safiyya, kasancewar ta juya masa baya ne sai hakan ya hana shi ganin fuskarta. "Piya" ya kira sunan ta yana kokarin juyo da ita ta fuskance shi amma sai taki, "safiyya ta" ya fada with that deep voice of his wanda ya kara zama deeper saboda baccin da yayi, tare da zura hannunsa a kasan cikinta yana kara jawo ta zuwa gare shi. Ta raba hannunsa da jikinta sannan ta mike da sauri, har tana vi kamar zata fadi ta shige toilet dinsa, ya dafe kansa da hannunsa daya tare da rufe idonsa for some seconds sai kuma ya tashi ya sauka daga gadon, ya duba agogo yaga some minutes to 12, dama jiya ma sai kusan hakan suka tashi, ya juya ya kalli toilet din, yana jin karar ruwa amma kuma sai jikinsa yake bashi cewa ba wanka take yi ba kuka take yi, ya mike ya bita toilet din, duk sanda ta shiga toilet takan rufe ne saboda ya san takura mata yace sai sun shiga tare, amma sai ya tarar yau a bude, ya tura ya shiga sai ya ji shower ce a kunne a dakin shower, ya karasa gurin ya tura kofar, kamar yadda yayi tunani kuwa a zaune take dirshen a kasa ta kunna shower din tana zubowa a kanta duk kuwa da cewa kayan baccin ta still suna jikinta, fuskarta a boye a tsakanin kafafuwanta, duk da baya ganin fuskar amma ya san kuka take yi. Yaji wani abu ya tsaya masa a kirjinsa, just 3 days ago ya zauna ya gama tsara mata alkawarin cewa ba zai barta ta sake yin kuka ba and she is already doing it. Ya shiga cikin shower din shima da kayan sa a jikinsa ya zauna a kusa da ita sannan ya jawo ta jikinsa. "Babe" Sai dai kuma sai ya rasa kalaman da zai yi amfani da su wajen rarrashin, "Babe please ki daina kuka mana" ya fada yana dago fuskarta tare da kissing idanunta da ya lura cewa hawaye ne yake fita daga ciki duk kuwa da cewa ruwan da yake zubowa a kan su yana wanke hawayen. Ta kwace fuskarta ta mike tsaye, forgetting cewa a jike jikinta yake, "ni ka rabu dani, bana son jin komai, a tashi ka tafi gurinta". Ruwan da ya jika ta ya saka kayan baccin ta marasa nauyi suka mammanne a jikinta suna bayyanar masa da dukkan surar ta, abinda ya gani ya rikirkita tunanin sa gabakidaya. Ya mike tsaye shima tare da jawo ta ya manna ta a jikinsa ruwan yana cigaba da sauka a kansu, a kunnen ta ya rada mata "am sorry Babe, I promise you, ba zaki kara kuka akan wannan issue din ba kinji? Please ki daina" ta fara kokarin kwatar kanta daga gare shi da niyyar cigaba da fushin ta, ya ki sakin ta da niyyar cigaba da lallashi, sai dai kuma a hankali sai lallashin ya chanja salo daga na kalamai ya koma na gangar jiki, jin ya fara daukan wata hanyar ta da ban ya saka ta cigaba da ture shi "ni ka rabu da ni, ka tafi gurin ta, kar ka kara zuwa guri na, kar ka kara yi min magana ma, kar ka ....... " Ya jawo fuskarta gare shi tare da hade bakin su cikin kiss mai cike da bayyana mata halin da zuciyar shi da gangar jikinsa suke ciki a kanta, tun tana kokarin kwatar kanta har ya samu nasarar zare dukkan wata laka da take jikinta, tun tana kokarin resisting kisses and touches din sa har ta fara mayar masa da martani ba tare da ta sani ba. A haka rarrashin yayi leading to something else wanda a karshe har sai da ya wajabtar da wanka akan su duk su biyun duk kuwa da cewa Gidado bai kai ga destination din sa ba yet. Amma a ransa ya san cewa ya kusa, kadan ya rage masa ya je din, ko a yanzu ma da ya takura da zata barshi ya je amma baya son ya takura din, baya son ta kuma alakanta wannan abin da feeling of being forced, ya fi son duk ranar da zai samu ya kasance da kanta ta bude masa kofa kuma ta gayyace shi. Ya kara karfin shower din tare da fara gabatar da wankan da ya wajaba a gare shi, ya juya yana kallon ta, ta dunkule a can karshe ta rufe fuskarta da hannayenta biyu da suka sha lalle, shi ya san ko ya ce ta taso suyi wankan tare ba zata taso ba dan kunyar sa take ji sosai, kunyar ce ma ta saka ta dunkulewa a guri daya kamar ball, sai dai, through all the kunya and all the rufe fuska yana iya hango murmushin da yake kwance akan fuskar ta, wannan murmushin kuma kadai ya ishe shi payment na hard work dinsa. Kunyar da yasan tana ji bata hana shi tsokanar ta ba, yayi directing ruwan shower din towards har ya fesa mata. Ta danyi kara tare da tare ruwan da hannayenta ta bude idonta kadan, sai kuma ta mayar ta rufe da sauri saboda abinda ta gani "na shiga uku. Menene haka ne? Wai kai ba ka jin kunya? Dan Allah ka saka kayanka ko kuma ka fita" yayi dariya "toilet dina ne, in kin isa ki tashi ki fita ke" amma kuma ya san ba zata iya tashi ba. Ko me zai yi mata ba zata iya tashi tsaye a gabansa a yadda take ba. "Dan Allah ka bari.... Dan Allah ka fita" ta cigaba da rokon sa a lokacin da ya cigaba da fesa mata ruwan avoiding her face dan kar ya hana ta numfashi, yace "ki taso muyi wanka to" ta girgiza kanta tana kara rintse idonta "I can't. Dan Allah kayi hakurj" yayi dariya, wai ita ce mai bashi hakuri, "ki kara bani hakuri to" "Allah ya baka hakuri, Allah ya huci zuciyar ka" "kice min Baby" "Baby na dan Allah kayi hakuri ka fita, ba zan kara tsokanar ka ba" yayi kwafa sannan ya mayar da ruwan kansa ya sake wankan da ya fara daga farko trying not to look at her dan kar ya koma ruwa, ya san yana bukatar concentration for abunda yake da niyyar yi yau. Ya gama wankansa sannan ya fita ya bar mata toilet din, ya shirya cikin sauri dan ya kusa makara masallacin sallar azahar, har ya fita daga dakin bata fito daga toilet din ba kuma ya san ta gama kunyar fitowa kawai take ji, da ya dawo daga masallaci ma bai same ta a dining ba kamar jiya da shekaran jiya, wannan ya sa ya debi abincin ya hau mata da shi har zuwa dakin ta, ya tarar da ita tana ta kokarin daura dankwali sai kamshi take, tana ganin sa ta warware dankwalin ta rufe fuskarta da shi, ya ajiye abincin tare da karasawa ya jawo ta jikinsa, ta fara ture shi yace "ko ki bude fuskar nan ko kuma ni kadai na san me zanyi miki" ya rada mata a kunne. Ta yi masa chakulkulin da ya saka ya sake ta da sauri, ta dauki abincin da ya ajiye ta ruga da gudu ta shige closet ta rufe kofa. Ya jima yana kallon kofar yana murmushi sannan ya fita. Shi kadai ya ci abincin sa a kasa yana jin kewarta, amma kuma bai matsa mata da sai ta fito sunci tare ba dan yana bukatar concentrating, ita kuma indai tana guri to dukkan tunanin sa a kanta yake tsayawa. And now he needs to think about something else. Wayarsa da take haske ya kalla, Safina ce dai, kira na kusan biyar kenan tayi masa a yau. Wannan ma barin sa yayi har ya katse da kansa bai dauka ba. Ya samu ya gama cuccusa abincin da kyar sannan ya shanye tea dinsa ya mike ya fita. Sai da ya zauna a sabuwar motarsa sannan ya dauko wayarsa ya tura wa Safiyya message "hey Babe, a fita. We will talk about it later". Yana tura mata ya tashi motar ya fita daga gidan zuciyar sa cike da tunane tunane. Hanyar daya gidan nasa ya dauka inda Safina take. Rabonsa da gidan tun ranar da za'a kawo Safiyya, ranar asabar. Dama tun ranar juma'a Mama ta kira shi tayi masa fada tas akan kin gaya mata da yayi cewa Safina bata gida tun ranar da aka daura auren sa da Safiyya. Shi dama tun ranar da aka daura auren bayan ya bar gidan su very late ya koma gida mai gadi yake gaya masa cewa ta fita daga gidan cikin tashin hankali, mai gadin was concerned cewa ko mutuwa aka Vi ko wani mugun abun da ban, sai ya fahimci cewa ta san abinda ya faru shine ta tafi gida. Tun daga nan kawai ya cigaba da harkokin sa bai neme ta ba bai kuma gayawa iyayensa ba ballantana su neme ta, amma a ransa yana ta jira yaji an kira shi ance Safina ko iyayen Satina sun ce ya sake ta, amma shiru babu wannan sakon, sal fadan Mama ne ya biyo baya tare da sanar masa da tayi cewa ta saka an dawo da Safina gidan ta. "ya kamata ka san halin da kake ciki akan yarinyar nan tun kafin ka daukar wa kanka nauyin da ba zaka iya saukewa ba" Mama ta fada a karshen fadan nata. Ya san abubuwa da yawa maganar maman take nufi, a ciki har da approval dinta na abinda ta san cewa yana ransa tun farkon auren na sa da Safina. Tabbas, tun ranar dinner din bikin su, ranar da ya fahimci dangantakar Safina da Safiyya, a ranar ya san cewa auren sa da Safina ba mai dore wa bane ba, ya san cewa zaman su tare wani abu ne da duk su biyun ba zasu ji dadin sa ba. Amma kuma ya kasa datse igiyar auren na su ne saboda iyayensa, saboda gudun bacin ransu, sai ya fara neman hujjar da zai basu dan su fahimce shi, aside her being related to Safiyya dan a lokacin yana ganin ba zasu dauki hakan a matsayin huja ba. Amma bai samu ba har abinda va faru tsakaninsa da Safina ya faru, sai kuma ga issue din cikinta, wannan duk ya kara hana shi rabuwa da ita. Yanzu kuma tun sanda cikinta ya zube tausayinta yake ji, duk da yasan ita din ba abar tausayi ba ce ba, gani yake ta rasa komai saboda soyayyar sa. Gani yake kuma idan bata yafe masa akan yanayin zaman da suke yi ba sai Allah ya kama shi da hakkin ta. Amma kuma ya sani, the more da ya cigaba da zama da ita the more alhakin ta da zai dauka ya dora wa kansa, wannan kuma shine maganar da Mama take yi masa. Sai dai kuma yana son rabuwar tasu ta zo da dadi yadda maybe zata iya yafe masa ko da ba yanzu ba, yana kuma bukatar dalilin da zai gaya wa kansa da kuma ita sannan da iyayen su a matsayin dalilin rabuwar aside her being Safiyya's step sister. Wannan ya sa ranar asabar din da za'a kawo Safiyya ya bi umarnin Mama yaje ya yi wa Safina siyayya, akwati guda uku ya cika mata da kayan sawa masu kyau da sauran kayayyakin amfanin mata, sannan ya biya ta gurin siyar da mota ya siya mata mota yar daidai misali aka biyo shi da ita zuwa gidan, Yana shiga ya saka mai gadi ya shiga da kayan cikin falonta ya ajiye, sannan ya shiga, bata falo, amma yaji motsinta a cikin dakin ta, ya je kofar dakin ya tsaya a bakin kofa yana kallon ta, hannayensa a cikin aljihunsa. Ta hargitsa dakin gabaki daya, ya kasa gane gyarawa take yi ko hargitsawa take kara yi. Ita kanta a hargitsen take. Ta juyo tana kallon sa, fuskarta gabaki daya kamar ba tata ba, har wani duhu ya ga tayi. "ango" tace tana yi masa wani murmushi da shi kansa ya san ba na gaskiya ba ne ba. "miji na kuma mijin kanwa ta. Wannan shine kirarin da zan ringa yi maka daga yau" ya juya kansa gefe yana kokarin hana kansa gaya mata wadda zata hana ta bacci yau. Ta cigaba "ita kuma daga yau sunanta kanwata kuma kishiya ta. Maciya amana, daga kai har ita". Ya danyi murmushi yace "daga mu har ke mun san cewa she didn't marry your husband, you married her boyfriend. Wannan shine cin amana" ta matso gabansa "really? Kuna da shaidar da zaku nuna min kan cewa na san kai saurayin ta ne sanda na aure ka? Kuna da shaida?" Bai amsa ba sai yace "me yasa kika dawo?" Ta danyi murmushi mai ciwo tace "me ya sa ba zan dawo ba? Ka manta kai mil na ne Habibi?" Ta fada tana kai hannu fuskar sa ta shafa sajensa ya danyi taku daya baya sai tace "kai miji na ne kuma ina son ka. No matter how much you hate me hakan ba zai cire min sunan matarka ba har sai ka sake ni da kanka. And you cannot do that saboda iyayen ka, shi yasa kaji dadi da na tafì gida ko ta kaina baka sake bi ba, a ranka kana murnar cewa na tafi na baku guri zaku ci amarcin ku son ranku ko? Ni kuma shi yasa na dawo, dan a raba amarcin da ni. Kar ka manta kwana uku ne, bazawara ce, dan ma dai at least ka dandana budurwar kaji dan haka yanzu zaka fi banbancewa sosai, zaka ware aya daga cikin tsakuwa, in ka gama kwana ukun sai ka dawo dakina, watakila zuwa lokacin ka fahimci gaskiya, in ma kuma baka fahimta ba ina bukatar ka dawo din ko kallonka ne in saka ka a gaba inyi tayi". Bai amsa duk wadannan maganganun nata ba sai ya juya ya koma falo yace "ki zo ina son magana da ke". A gaban kayan da mai gadi ya ajiye ya tsaya, ta fito sai ta tsaya itama tana kallon kayan tana kuma kallon sa, ya nuna mata kayan da hannun sa. "ga kaya nan. Mama tace ana yi a al'ada" ya ciro key din motar ya dora akan kayan "ga wannan, it is a gift from me to you. I know we have been on a wrong foot throughout our days together amma ina fatan maybe watarana we will forgive each other". Ya daga kai yana kalion ta, ga mamakin sa sai yaga hawaye suna bin fuskar ta, ya danyi gyaran murya yace "akwai abinda kike bukata?" Ta dago kai tana kallon sa tace "abinda nake bukata? Kamar me fa?" Ya dan daga kafada "foodstuff, cleaning things, anything dai" ya juya kanta tace "what of mijina? Idan miji na nake bukata kuma fa?" Ya sauke ajjiyar zuciya bai ce komai ba, ta tako zuwa inda yake "ba'a kawo ta ba ai, dan haka yanzu ma a dakina kake, me zaka yi idan nace kai nake bukata a yanzu?". Ya zaro ATM card ya ajiye a kusa da key din motar yace "dan kina bukatar wani abu ki cira kudi ki siya, 2728 shine pin din". Daga haka ya juya ya fita ya bar gidan, bai sake kuma waiwayar gidan ba duk kuwa da kiran da take ta zabga masa a waya kullum sai yau, three days later. Yana shiga gidan yayi packing yana amsa gaísuwar da maigadi yake yi masa sannan ya fita ya shiga bangaren sa, ya tsaya yana karewa dakin na sa kallo, thinking about a lot of things, thinking about abinda ya kamata ya dauka a dakin da kuma wanda baya bukata. Sai dai bai dauki komai din ba, ko zai dauka ba yanxu ba. Ya zauna akan study yabl6din da yake dakin ya dauko wata takarda sannan ya dauki biro yayi rubutu a cike sai ya ninke ya saka a cikin aljihunsa sannan ya dauki wayarsa ya kira number din Abba suka danyi magana kadan sai ya kashe ya mike ya tafi bangaren ta. Ya tarar da ita tana ta gyara gyare, da alama deep cleaning take yi wa gidan, ya yi sallama sannan ya tsaya a bakin kofa ya saka hannayensa a cikin aljihu, mai aikin ta ta gaishe shi sannan ta shiga ciki da sauri, ba'a jima ba Safina ta fito tana gyara dankwalin kanta. Yayi mata murmushi, sai yaga mamaki ya bayyana a fuskar ta. Maybe bai taba yi mata murmushin gaskiya ba. "Sannu da zuwa" ta fada indicisively, "I thought ba zaka z0 ba. Nayi ta kira baka dauka ba" ya daga kafada, "You didn't need to keep calling" ta karasa shigowa tana kallon fuskar sa da take dauke da murmushi da kuma annurin da ya kasa boyewa, kowa ya kalle shi sai yaga annurin angonci a tare da shi, "I thought ba zaka zo ba shi yasa nayi ta kiran ka. I thought I need to involve our parents…." "Cut the threats" ya fada, "sit. Magana na zo zamuyi" ta zauna kamar yadda ya bukata akan kujerar zaman mutum biyu tana kallon sa, yanayin da ta fuskanci yana ciki shine abinda tayi burin samu a rayuwar auren su, shine kadai abinda take son samu, not mota ko kudi.... Was it too much to ask? Sai ya karaso, and ga mamakin ta sai ta ga ya zauna akan kujerar da take zaune akai, it was the closest they get tun da aka daura musu aure except for that night. And to top it all sai ta ga ya kama hannun ta ya rike a cikin nasa, still with that smile on his face yace "Safina, Magana nake so muyi. Please ina bukatar attention dinki. Ina son muyi first reasonable magana as a couple. Ina son mu samu understanding, Ina so mu samu matsaya a auren mu" ta daga kai ta saka idonta a cikin nasa, within the first second ta gana narkewa, duk wasu makaman yakinta suka zube daga hannun ta suka barta ita kadai, daga ita sai zuciyarta sai kuma wadannan idanuwan nasa da yake kallonta da su. "Can we talk, please" ya fada a kokarin dawo da ita cikin nutsuwar ta. Ta saka daya hannun nata ta kara rike hannun sa da ya rike nata da shi, ji take kamar za'a saka hannu a zare mata shi, ji take kamar in ta sake shi zai bace ya barta ta cigaba da miserable zaman da take vi ita kadai a rayuwar da ko kallo bata ishe shi ba. Ta gyada kan ta da sauri gain still jiran amsar ta yake yi. Yayi ajjiyar zuciya "Okay. Here is the thing. We have started on a totally wrong foot a cikin auren mu, kuma akan wrong feet muka yi ta tafiya har yau kuma akai muke. I want to change our relationship. Dan wannan da muke kai babu inda zai vi leading din mu to sai destruction. Haka ne?" Ta sake gyada kai tana jin kamar a cikin kwakwalwar ta yake yi mata maganar, kowacce kalma ta sa tana samun guri tana zama a cikin kanta, Ya cigaba "okay, Tunda mun amine muna bukatar chanji then next thing shine thing shine mu yi letting go of the one we have tunda mun fahimci babu inda zai kai mu sai wahala. But before that, ni dai personally, ina so in gaya miki cewa duk abubuwan da kika yi min, wanda na sani da wanda ban sani ba idan da akwai, na yafe miki. Duniya da lahira. Kuma on the other hand, ina neman yafiyar ki ta abinda ni navi miki intentionally ko unintentionally" ya sake fadada murmushin sa,"na san navi miki abubuwa da yawa, some of them I am even ashame of them. Ina fatan zaki yate min, ko da ba yau ba, ko watarana ne" ta danyi shiru tana studying, ta kasa placing kalamansa at the exact spot da ya kamata ta saka su. Abinda dai is clear to her shine Muhammad ne, Habibin ta, a zaune a gabanta hannunsa rike da nata da kuma murmushi akan fuskar sa yana rokon ta gafara akan abinda yayi mata, that is more than abinda take roka a cikin addu'arta. Ta yi masa murmushi "a lot of things have happened. Most of which nice na jawo su. Kuma ko a lokacin ma in ka tuna ai ina gaya maka cewa na yafe maka, saboda ina sonka, na sha gaya maka ba zan iya rikon ka a raina ba dan bana son Allah ya kama ka a kaina" ta fada tana shafa gefen fuskarsa da hannun ta daya, dayan still yana rike da hannunsa. Yace "yes, da farko kenan. Amma daga baya nayi manyan laifuka ai, avoiding your bed, slapping you, and the baby......... Na san it wasn't entirely my fault but da ace ban bari emotions dina sun rufe idona ba maybe the accident wouldn't have happened. Kiyi hakur'" ta sunkuyar da kanta tana jin hawaye yana taruwa a cikin idonta, taso cikinta kamar ranta, rashin cikin nan was the saddest thing that has happened to her a rayuwar ta. Ta daga kai ta kalle shi tace"Allah bai yi da ma zai zo duniya ba. But yanzu ka yarda cewa naka ne? Ka yarda kai kadai na sani ban san kowa ba?" Ya gyada kansa yana jin zuciyar sa tana breaking ace "Na yarda. Ko a lokacin ma na yarda. Na fadi maganganun ne cikin bacin rai. Kiyi hakuri" ta yi murmushi, a ranta tana kara tabbatar wa da kanta abinda zuciyar ta ta gaya mata tun farkon shigowar sa, ya banbance tsakanin aya da tsakuwa, ya gama chasing tsakuwar ya dawo gurin ayar "na hakura" ta fada tare da ajjiyar zuciya, tabbas komai yayi farko zai yi karshe. "Na hakura, Allah ya bamu wasu masu albarka" yayi murmushi yace "Nagode sosai. This really means a lot kuma ba zan taba mantawa ba". Suka yi shiru suna kallon juna kowa da abinda yake zuciyar sa, sai ta daga kanta tana kokarin hade bakin su. Ya dan matsa kadan sannan ya mike tsaye. "Get your veil. Zamu je wani guri yanzu" ta mike tana kallon sa, gabanta yana faduwa amma bata gane ina yake nufi ba. Basu taba fita outing as a couple ba, maybe wani guri zai kai ta, maybe kasuwa suyi siyayya, maybe gidan abokin sa, maybe...…. Alot of maybes. Sai kuma ya kalli agogon sa yace "bara inje inyi Sallah, Ki same ni a mota", Itama sallar tayi. Amma hankalin ta baya tare da ita. Babu abinda take yi sai juya maganganun sa a ranta, Amma zuciyar ta taki barin kwakwalwar ta tayi digesting maganganun ballantana ta fitar da amsa. Tarin soyayyar sa ta rufe reasons a tunanin ta. Tana gamawa ta kara gyara jikinta sannan ta saka mayafin ta ta gayawa mai aikin ta cewa zata je unguwa ta dawo. A mota ta same shi yana waya. Tana shigowa ya karasa wayar sannan ya tayar da motar suka tafi. Ga mamakin ta sai taji yana mata hira a hanya, yana nuna mata gurare da kuma bata labarin da ya shafi gurin, har da dariya yayi mata. Sai da suka yi nisa sannan ta gane inda suka dosa, gidan Daddy. "Me zamuyi a gidan Daddy?" Ta tambaye shi "zamu hadu da iyayen mu ne muyi magana akan relationship din mu" tayi shiru tana digesting maganar "I thought mun gama maganar dazu" yace "yes, but they need to know, ko ba haka ba?" Ta girgiza kai "we are not kids. Bama bukatar gayawa kowa komai akan auren mu. Besides, Daddy ba babana bane ba. Ni baba na ya mutu" ya juyo da sauri ya kalle ta sai ta dauke kai gefe, bai kara cewa komai ba dan bayan gudun kar ta fadi wata mai zafi akan Daddy har ya kai ga mayar mata ya bata duk shirin da yayi, Jin bai yi magana ba sai ita ta cigaba "baya so na, Ya zabi yarsa a kaina, Idan ya dauke ni ya babu ta yadda za' ayi ya aura maka Safiyya. Ya kori yaya Mustapha ma daga gidansa after all the years da ya dauka yana bauta masa. Bai damu da bacin ran Mommy ba. Bai damu da mu ba" ta karasa tana dan daga murya. Still bai ce komai ba, har suka je suka yi packing, kamar yadda yayi tsammani, ya ga motar Daddy a gurin shima. Ya fito yace mata tazo su je, ya lura gabakidaya ta rasa composure din da ta samu sanda suka yi magana a gida, amma sai ta samu kanta da binsa suka shiga ta kofar waje zuwa falon Daddy, ta ga Abba a gurin sannan Mommy, ko kallon ta Mommy bata yi ba, dama tunda ta koma gidan Muhammad ko ta kanta bata bi ba ko ta kira ta a waya bata dauka, a gurin Safina sai take gain fushine kawai Mommy tayi zata huce ne daga baya. A bangaren Mommy kuwa tun ranar da Hajiya ta gaya mata Maman Muhammad ta turo da yan'uwan ta sun bada hakuri sun kuma gaya mata cewa su basu san cewa Safina tana gida ba, Muhammad bai fada musu ba, sannan kuma sun nemi tafiya da Safina, Hajiya taso ta hana Safinan komawa, taso a bari a gama bikin Safiyya sannan iyaye su hadu aji makomar auren Safinan amma sai Safina ta dauki mayafi ta ce ita komawa zata yi. Mommy tayi niyyar binta a ranar ta jawo ta ko da kuwa a kasa ne ta raba ta da gidan, amma daddy ya hana ta, a cewar sa Safina needs to learn on her own, idan suka tirsasa mata rabuwa da Muhammad zata ce su suka raba ta da shi dan basa son ta sun fi son Safiyya. Dan haka ta ja gefe take jira, kamar yadda sauran iyayen suma suke jira, sai yau da Daddy yace mata abban Muhammad yace zasu zauna akan maganar Safina da Muhammad sannan ta zo ta zauna din dan taga yadda lamarin zai kare. Muhammad ya gaishe su daya bayan daya, sai Safina ita ma tayi haka. Daga Muhammad din har Safinan Mommy ba ta amsa musu ba. Suka zauna a kasa yayin da iyayen suke akan kujeru. Sai kuma Muhammad yaji ya rasa me zai ce har sai da Abba yayi magana "kace mu zo kuma kayi shiru" Muhammad yayi dan gyaran murya yace "uhmm. Dama muni magana ne da Safina, Mun samu fahimtar juna kuma mun yafe wa juna duk abubuwan da suka faru a baya, Muna so mu sake bawa relationship din mu second chance mu ga yadda Allah zaiyi da mu. Shine muka z0 mu gaya muku", Sal ya ga kowa ya saki baki yana kallon sa, har ita kanta Safinan, dan da taga sunzo nan har ta fara sarewa akan abinda yake shiryawa. Abba yace "Muhammad, Look at me. Are you sure? Duk maganar da muka yanke yanzu anan ita ce final. Ka fahimta?" Muhammad ya gyada kai "na fahimta Abba. Nima ba zan kira ku ba idan har ban tabbatar da decision dina ba" ya juya yana kallon Safina da take ta zabga murmushi kanta a kasa. Sai kuma ya cigaba "a ganina everyone deserves a second chance, I mean Safina tayi laifuka kamar yadda nima nayi, idan har zata iya yafemin nima me zai hana ba zan yafe mata ba? A bisa alkawarin cewa ba zamu sake maimaita laifukan mu ba. Misali, ni yanzu nayi alkawarin cewa ba zan sake wulakanta Safina ba, ita kuma tayi alkawarin cewa ba zata sake yin karya da kazafi da munafunci ba" ya fadi haka yana kallon Safina da ta dago tana kallon sa ita ma yace "ko?" Ta kalli iyayen su da suke kallon ta sai ta gyada kai, amma hakan bai ishe shi ba sai ya sake maimaitawa yace "kinyi alkawarin ba zaki sake yin karya, ko kazafi, ko munafunci a cikin auren mu ba?". Jikinta ya bata cewa something is wrong, amma ya nannade ta da jijiyoyin jikinta dan haka tace "eh. Nayi alkawari" yayi murmushi "shikenan. Muna neman a saka mana albarka mu koma gida. But before that I just need to ask Safina one question. Safina, did you or did you not know cewa ni saurayin Safiyya ne kafin ki tura picture dina blog?". Tambayar ta zo mata a bazata, and her whole world came crashing down on her head. Ta dago kai tana kallon sa "what?" Ta tambaya, a take ya maimaita mata tambayar "did you or did you not know cewa ni saurayin Safiyya ne kafin ki tura picture dina blog?". Tayi shiru tana kallon sa sannan ta fara bin iyayen su da kallo, interestingly gabakidaya ita suke kallo suna jiran amsar ta, a take ta fahimci trap Muhammad ya haka mata, already kuma ta fada a ciki, yanzu so far bai sake ta ba saboda bashi da wani laifin da zai makala mata yace shine dalili, shine yake so ya binciko wannan maganar a gaban iyayensu a kuma sake ta saboda ita, ita kuma ba zata bar hakan ta faru ba. Never. And she automatically gets into her defensive mode. "Muna jin ki" Mommy ta fada, maganar ta ta farko tun da suka shigo, maybe yanzu da ta fahimci cewa sakin ta za'a yi shine ta fara murna. Safina ta kalle ta sannan ta kalli Abba tana girgiza kai, ta san shine way out dinta a wajen tunda Mama bata zo ba, ta san muhammad baya taba kaucewa maganar iyayen sa "ni wallahi ban san saurayin ta bane. wallahi bata taba nuna min shi ba. Bata taba hada mu ba" Muhammad yace "nasan wannan. Ita kanta Piya...... .. Uhmm I mean Safiyya ta gaya min bata taba nuna miki ni ba, kawai dai tambayar ki nake yi ko kin taba ganin hoto na a wayarta, ko kin dauki hoto na a wayarta. Or something like that?" Direct ta amsa "wallahi ban taba ganin hoton ka a wayar ta ba. Wallahi.... "Ya daga mata hannu, "Magana ta kare, bani wayarki" ta juya ta kalli Mommy sannan ta kalle shi, "waya ta kuma? Me zaka yi da wayata?" Ta fada cikin mamaki, bai amsa mata ba sai ya miko mata hannu, ta dauko wayar daga cikin jakarta ta bude ta mika masa, a ranta tana lissafin cewa in dai laifi yake nema ya makala mata ba zai samu ba, dan babu wani abun laifi a cikin wayarta. Muhammad ya fara scrolling through tarkacen hotunan da suke cikin wayar, ba shi da tabbas din me yake nema amma a ransa yana jin cewa zai samu, bai san wanne hoton bane ba and it has been more than two years but a yasan how obsessed Safina is with him, baya jin zata ¡ya rabuwa da hotonsa a cikin wayarta. Ya jima gana scrolling, yayin da su kuma suka cigaba da kallon sa suna jiran suga abinda yake nema. And he saw it bayan har ya fara fitar da rai. His picture, a tsaye a jikin motar Safiyya a cikin makaranta, hannayensa a cikin aljihunsa. Ya na ganin hoton ya tuna shi. Safiyya ce ta dauke su selfie tare shi da ita. Yayi murmushi yana tuno da yadda ta so hoton a lokacin, ya tuna har saka shi tayi a matsayin screen saver din wayarta for a while. Sai kuma ya kara kallon hoton and he realized something, hoton ya nuna cewa an dauke shine a jikin screen din wata wayar sannan aka yi cropping, akayi cropping out Safiyya from the picture. Ya girgiza kansa sannan ya mika wa iyayen su hoton. Kamar yadda ya gane suma haka suka gane, har da date da time gashi nan ya fito a jikin hoton. A hankali yace "like I said. She didn't marry your husband, you married her boyfriend" ta sunkuyar da kanta kasa tana jin hawaye yana bin fuskar ta sai ya dauko takardar da take cikin aljihunsa ya ajiye mata a gabanta sannan yace "this is not because of Safiyya. It is because of you, halin ki da yanzu duk muka tabbatar ba zaki daina ba, ba zan iya zabawa yaya na uwa mai hali irin naki ba. Ina yi miki fatan alkhairi". Ta daga kai ta kalle shi, yayin da shi kuma ya mike tare da yiwa iyayensu sallama ya fita. Babu wanda ya tsayar da shi a cikin iyayen nasu ballantana har su hana shi vin abinda ta tabbatar ya riga ya aikata. Abba ne ta tashi ya dauki takardar da take gabanta ya karanta sannan ya mika wa Daddy sannan yayi musu sallama tare da fatan alkhairi sannan ya fita shima kamar yadda dan na sa yayi. Daddy ne ya sake mika mata takardar, ta bude ta karanta rubutu kamar haka. "Ni Muhammad Lawan Muhammad. Na saki matata Safina Ibrahim saki daya. Ina yi mata fatan alkhairi". Maman Maama✍🏻 [07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: Assalamu alaikum Gaisuwa tare da fatan alkhairi. Naga a lot of complains din ku akan kuna son a kara tsahon labarin Safiyya. My initial plan was to conclude the book in the next three episodes. A yanzu dai bana jin zan iya kara episodes, sai dai idan zan dauki break of like two weeks in kammala da was muhimman abubuwan da suke jira na idan na gama Safiyya, in yaso in na gama su sai in dawo mu cigaba. So, kamar kowanne littafi na, wannan karon ma zan bawa readers damar voting yadda karshen labarin zai kasance. 1- in cigaba bisa yadda na tsara in kammala in 3 episodes 2- in kara jan labarin a kara yawan episodes amma zan dauki break din two weeks. Ya kuka gani???? Idan 1 kika zaba kiyi reacting 👍 Idan 2 kika zaba kiyi reacting 🙏 Any other emoji is invalid vote 😀 Za'a gama voting in two days. [07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: Safiyya…… Falon yayi shiru bayan fitar Muhammad da Abba. A hankali kuma sai sheshshekar kukan Safina ya fara mamaye shirun. Daddy ya sunkuyo da kansa yana kalion ta, tana zaune kanta a kasa hawayen ta yana diga akan farar takardar da take hannun ta, takardar da ta yanke dukkan alakar da take tsakanin ta da Muhammad. Ya daga kansa yana kallon Mommy wadda har lokacin kofar da Muhammad da babansa suka fita daga ciki take kalla. Fuskarta da wan irin yanayin da ya kasa placing. Sai kuma ta juyo a fusace tana kallon Safina tace "zaki yi min shiru a gurin nan ko sai nazo na shake ki kin daina numfashi?" Bata yi shirun ba kuma bata ce komai ba, sai ma kukan nata da ya karu. Mommy ta mike da sauri tayi kanta duk kuwa da maganar da Daddy yake yi mata akan ta dakata, ta kai mata mari sai Safina ta sunkuyar da kanta dan haka marin ya sauka a saman kanta, sai ta kwanta a gurin tare da kara sautin kukan ta "dama haka kuke so ai. Gabakidayan ku haka kuke so. Babu wanda yake so na. Babu wanda yake son farin ciki na. innaliliahi wa inna llaihir rajiun" Mommy ta saka kata ta dake ta cikin dacin zuciya sal kuma ta rike kafar tana cije baki "Daddy ya dan daga murya cikin kokarin ganin Mommy ta saurare shi "Sa'adatu. Kar ki dake ta. Da me zata ji?" Mommy ta dawo ta zauna tana rike kafarta yayin da Safina ta cigaba da kukan ta, Mommy ta kama fada, first time da tayi fada in days "ba ma son ki din, na ce bama son ki din. Ya za'a yi mu so ki alhalin ke ba kya son kanki? Ya za'a yi mu damu dake bayan ke baki damu da kanki ba? Da kina son kanki da babu yadda za'a yi tun farko ki dama wa kanki wannan salalar tsiyar. Da ba zaki gina foundation din auren ki akan karya da yaudara ba, da ba zaki zubar da mutumcin ki da kimar ki a idon mijin da zaki aura da kuma yan uwansa ba. Me yasa ba zai sake ki ba? Me yasa iyayen sa ba zasu goyi bayan ya sake ki ba? Me yasa ba zai ki zabar ki a matsayin uwar yayansa ba? Waye zai so mace mai irin halin ki ta tarbiyyan tar da yayan sa?" Safina ta mike zaune tace "Saboda Safiyya ne Mommy, Wannan duk excuses ne yake creating amma saboda Safiyya ne, Ita ta saka shi ya sake ni.Shi ya gaya min da bakin sa yace komai yake yi saboda Safiyya yake y". Mommy tace "idan ya sake ki saboda Safiyya sai me? Ke saboda me kika aure shi? Ba saboda Safiyya ba ne ba?" Satina ta fara girgiza kai "ba zan iya rabuwa da shi ba Mommy, Nina hakura zan zauna da Safiyya kuma ba zan kara ce mata bazawara ba. Na san akan hakan ta saka shi ya zo ya yaudare ni ya saka nace na yafe masa sannan ya sake ni. To wallahi ban yafe ba. Allah ya isa na, Sai Allah ya saka min. Kuma wallahi sai ya mayar da ni .....”. Kuka take daga dukkan alama ma vata cikin hayyacin ta, Mommy bata san sanda ta mike ta sake rufe ta da duka ba. Sai da Daddy ya danna intercom ya kira Hassan da yake kusa sannan ya zo ya rike Mommy wadda take ta fada a jikace, daga ganin ta zaka gane ranta a matukar bace yake, fadan ma da kyar take yi tana rike kirjinta "so kike ki kashe ni Safina? So kike in mutu ki huta tunda dama kince ba na son ki ai. To wallahi gidan nan zaki bari. Ki tattara ki koma gurin wadanda suka daura miki auren tunda sune masu son ki sai su mayar miki da auren tunda kin ce sai kin koma, Sai in gani idan igiyar auren a hannun su take ko a hannun ki ballantana ku mayar da shi. Kuma wallahi kinji na rantse, ko da yaron nan ya dawo da kansa, in kika sake kika koma gidan sa babu ni babu ke har abada sai dai ki nemi wata uwar ba ni ba, kinga sai ki kara tabbatar wa da cewa bana son ki,.…” Hassan yayi ta kokarin rarrashin Mommy, Yadda duk ta tayar da hankalin ta sai yake jin nashi hankalin ya tashi. Dama daga shi har Hussein tun ranar da Daddy ya zaunar da su yayi musu magana akan auren da ya daura wa Safiyya, mijin da ya daura mata auren da shi da kuma dalilin da yasa yayi haka suka san cewa wannan ranar zata zo. And su babbar damuwar su da zuwan anar shine mahaifiyarsu, suna sonta sosai ba sa son bacin ranta kuma sun san dole abinda ya shafi Safina ya shafe ta, su ma kuma ya shafe su. Cikin gida ya kama Safina ya shiga da ita tana ta kuka da farar takarda a hannun ta. Yana tafiya Daddy ua jawo kujerar sa wajen Mommy yana kokarin kwantar mata da hankali, ta girgiza kai "ba zan iya da wannan abin kunyar na Safina ba. Katsina zan mayar da ita gurin wadanda suka daura mata aure ba tare da bincike ba. In na barta a gidan nan watarana zan kashe ta ko kuma ita ta kashe ni da bakin cikin ta*. Ya girgiza mata kai "in kin mayar da ita Katsina ta yaya zamuyi gyaran tarbiyyar ta? Kina tunanin su zasu gyara ta? Kina gani dai a gaban mu yaron nan yay mana proving cewa akwai matsala a tarbiyyar da muka bata. It is not too late. We can help her" ta sake girgiza kai "ba azo stage din da zamu taimaka matan ba ai., A yanzu tana bukatar rayuwata fara koya mata darasi kafin mu mu dora daga inda rayuwar ta tsaya, The way she is obsessed with yaron can zata iya daukan mayafin ta ta koma gidan sa tace ta mayar da kanta. Gwara tayi nesa da mu. Gwara tayi nesa da shi". Daga haka ta mike ta yi cikin gidan, ya bita da kallo har ta shige yana jin tausayin ta a ransa. Sunyi mistakes, gabakidayan su sunyi mistakes, sai dai yana rokon Allah ya basu ikon gyara mistakes din su akan Safina da Mustapha kamar yadda ya bashi ikon yi akan Safiyya. Amma kuma a ransa bai ji komai ba gane da sakin Safina da Muhammad yayi, yanajin cewa hakan shine mafi alkhairi a gare su baki daya. Zama da wanda ba ka so ba karamin ciwo ne da shi ba, and zama da wanda baya son ka is even more painful. Sai ya dauki wayarsa, yana lura da yadda numfashi yake kara yi masa nauyi a cikin kwanakin nan, and for the first time in weeks yay dialing number din Mustapha. Yayi nazari sosai akan case din Mustapha da Safiyya, ya fahimci cewa Mustapha yana da laifi kamar yadda su ma shi da Sa'adatu suke da laifi a cikin lamarin. Bata jima tana ringing ba Mustaphan ya dauka, a hankali yace "Daddy" sai kuma yayi shiru, Daddy ma yayi shirun, har lokacin yana jin zafin abinda Mustaphan yayi kokarin yiwa tilon yarsa, amma kuma shima Mustaphan yana jin sa a ransa kamar shi ya haife shi. "Ka zo gida... Daddy ya fada "kazo gida akwai maganar da zamu y". Daga haka ya katse kiran. Sai bayan da yayi sallar magrib aka bashi abinci yaci sannan Mustapha ya zo gidan. Yayi sallama ya shigo dakin amma sai ya tsaya a bakin kofa kansa a kasa yana kallon kafafuwansa. Daddy ya bishi da kallo, yayi baki, duk ya kara bushewa, duk babu gayu da daukan wankan nan. "Zo nan" Daddy ya fada masa with authority, half expecting him to turn around ya koma shima yace ai Daddyn ba babansa ba ne ba kamar yadda Safina ta fada dazu, amma sal ya ga ya taho din, ya 2o ya zauna a gabansa a kasa sannan yace "Daddy barka da yamma" Daddy yayi shiru yana studying dinsa. Tun yana shekaru goma yake hannunsa, yanzu gashi yana neman cike shekaru talatin a duniya, and through all those years, ba zai ce baya yi masa laifi ba tunda ya san ko yayan da ya haifa suna yi masa laifi, amma abinda ya sani shine yana yi masa biyayya. "Ina so muyi magana da kai. Ina so kuma in na gama maganar ka bani amsar abinda ka fahimta a maganar tawa da kuma abinda kake tunanin zaka yi a matsayin ka na babban da a gidan nan". Sai ya bashi labarin komai akan alakar da take tsakanin Safina, Safiyya, da Muhammad. Ya ga alamar ran Mustapha ya baci "ni ba haka ta ce min ba Daddy, ba haka Safina ta gaya min ba. Cewa tayi min a gurin dinner dinta suka hadu kuma tun daga nan suke in a relationship, tace a wayar ta ma Muhammad din ya dauki number din Safiyya" Daddy ya daga kafada yace "karya ta yi maka. Tana da karya sosai tun yarinta har karyar ta zama habit din ta, Yanzu ma akan halin ta na karya ne mijin ta ya sake ta" suka yi shiru sai Daddy ya kara da cewa "me kake tunanin za'a yi akan lamarin ta?" Mustapha ya danyi tunani sannan yace "ta ce kowa baya son ta har Mommy. A barta ta je Katsina ta kwana biyu sai ta gane ma'anar so din, zata dawo da kafafuwan ta za kuma ta gane gata ake yi mata. Yanzu idon ta ya rufe da soyayya ba zata ji reasons ba. Sannan aje a kwashe kayanta daga gidan Muhammad as soon as possible, dan a tabbatar mata da cewa ba zata koma ba. Duk randa Allah ya sa ta dawo daga Katsinan ta kuma gane gaskiya sai ayi mata afuwa a karbe ta, a kuma mayar da ita makaranta ta karasa karatun ta. Hakan zai taimaka mata wajen moving on. Hakan kuma zai bude mata kofar wasu chances din". Daddy yayi shiru yana kallon sa. Sai kuma yayi ajiyar zuciya. Shi bai fiya son tarbiyya ta hanyar horo ba, ya fi gane tarbiyya ta hanyar soyayya da kuma jan yaro a jiki. Amma kuma kamar sun fi shi gaskiya. She needs to learn her mistakes by herself. Amma kuma yana tsoron kar a hure mata kunne a can, kar maimakon gyaruwa ta kara lalacewa a can. Amma sai kawai ya hakura, "Okay. Shikenan. Allah yasa hakan shi ya fi alkhairi. Ta shi kaje". Sal dal kuma sai Mustaphan ya kasa tashi ballantana ya tafi din. Ya cigaba da zama idanunsa a kasa, "Daddy " ya ambata tare da dago kai yana kalion Daddy, "Daddy ban san abinda nayi ba. Ban san abinda aka ce nayi ba, Daddy ko me nayi dan Allah kayi hakuri",. Daddy ya sake yin shiru, ya riga ya yafe wa Mustapha abinda yayi din, amma har yanzu yana jin zafin a ransa musamman idan ya tuna cewa da ace Safiyya ta yarda, maybe da matarsa kawai zai mayar da ita a gidan har sai randa asiri ya tonu. Ya dauko wayarsa yana danne danne har ya binciko video din da ya riga yayi saving. Sai ya juya wayar ya nuna wa Mustapha. "Dan taya ni ganin wanna video din". Mustapha ya karba a ransa yana tunanin ko menene, sai yaga abinda bai taba tsammani ba, ya kuma ji abinda bai taba tsammani ba. Cikin sauri ya danna power din wayar ya katse videon tare da kashe wayar gabakidaya, as if yin hakan zai goge maganar daga memory din Daddy. Sai kuma suka yi shiru, Mustapha yana fatan kasa zata tsage ya shige cikin ta. Daddy yayi magana "ka bani mamaki Mustapha. Har bragging nake yi cewa ba ni da matsala da kai. Har kokarin tursasa yarinyar nan ta aure ka nayi ina ganin kamar kai ne kafi kowa dacewa da ita. Ka gaya min idan da akwai wani laifi da nayi maka da zaka yi min wanna cin mutuncin a cikin gida na. Ka gaya min" ya karasa yana kokarin daga muryarsa da bata fitowa sosai. Mustapha ya san da Daddyn da ne da yanzu maybe jikinsa yayi tsami, Amma sai ya kasa daga ido ya kalle shi, to da wanne idon zai kalle shi ma? Instead sai ya fara girgiza kansa, amma kuma bakin ma ya kasa yin motsi ballantana ya bada hakuri, to mai zai ce masa? Wannan wanne irin abin kunya ne haka. Ya lura da video din cctv ne, ya kuma fahimci cewa ba Safiyya ce ta tona masa asiri ba. Kamar yadda ya fahimci cewa ba kwace mijin Safina tayi ba. Ya fahimci Safiyya bata da laifi, sai ma tarin kaddarori da suka yi ta saukar mata one after the other. And he didn't do anything to help her matters at all. Daddy ya cigaba da magana "ita Safiyyan da kayi kokarin zalinta, ita ce mai roko na kullum akan in yafe maka in dawo da kai gidana, tace ba ka da wani gida sai wannan. Yace nan ne gidan ku. Amma kai ba ka dauke ta kanwa ba. Da ka dauke ta kanwa da ba zakayi niyyar aikata mata wanna mummunan abin ba" Mustapha yayi magana at last "Daddy ba yanzu ba ne ba wallahi. Wallahi ba yanzu bane ba. Dan Allah ka fahimta Daddy. Ban san me zance maka ka fahimta ba. Wallahi nayi nadama tun dadewa, Dan Allah Daddy kayi hakuri" shiru Daddy yayi sannan yace "a hakura ai, Da ace ban hakura ba da ko gate din gidan nan ba zaka sake gani ba. Yanzu ka debo kayanka ka dawo dakin ka. Sannan ka ajiye wannan girman kan ka je ka karbi aikin da Safiyya ta baka. Ka kuma hada kan kannenka ka rike su ka gyara tsakanin su. Sannan ka kula da mahaifiyar ka. Tashi ka tafi". Mustapha ya mike, not knowing what to think, ya kusa fita Daddy ya kira sunan sa, ya juyo amma still bai kalli Daddyn ba sai yace "kuma ka samo mata kayi aure. As soon as possible". A bangaren Muhammad tun sanda ya fita daga gidan sai ya dauki hanyar gidan su, ya san dole yana bukatar suyi maganar shida iyayen sa, amma kuma hankalin sa gabakidaya yana kan Safiyya da ya bari a gida. Bai jima da yin packing a gidan ba Abba ya shigo shima. Sai ya jira shi yayi packing sannan suka shiga cikin gidan a tare, Kamar yadda suka yi tunani Mama tana ta akin jera musu abincin dare, tayi wa mijin nata sannu da zuwa sannan ta juya ta na kalion Muhammad da ya sunkuyar da kansa kasa yana shafa gashin kan sa, ta san akwai magana. Ya gaishe ta amsa tare da tambayar sa lafiyar Safiyya da kuma Safina "lafiya lau" kawai ya amsa mata yabi bayan Abba suka fara shirin alwalar sallar magrib. Bayan ya gama alwalar ya kira wayar Safiyya, tana ta ringing bata dauka ba. "damn it" ya dan fada a hankali. Sai ya tura mata message "Babe ......... call me please" sannan ya bi bayan Abba suka tafi masallaci. Suna fita waje Haidar yana shigowa, shima sai yabi bayansu suka tafi tare. Bayan sunyi Sallah ya dauka zaman ba zai yi tsaho ba, amma sai yaji magana ta mika, Abba ne yayi wa Mama bayanin abinda ya far da kuma hukuncin da Muhammad din ya yanke, "Allah ya sa haka shi yafi alkhair'" kawai tace tare da tashi ta fara zubawa mijin na ta abinci. A ranta tana jin feelings dinta blank akan abinda ya far, a wani bangaren ma godiya tayi ga ubangiji da yasa babu rabo a tsakani, tana kuma fatan wannan ya zamo karshen wahalar dan nata a bangaren aure, ya samu nutsuwa shima ya samu farin ciki, ko burinta zai cika na ganin ya zama abin alfahari ga kowa. Ta zubawa Muhammad abincin shima, ya dauka ya fara ci yana ta kallon agogon hannunsa, da sauri ya cinye abincin yana son yayi musu sallama sai yaji sun dauko wata maganar kuma. Maganar sabon aikin da ake nemawa Haidar da kuma filin da aka siya masa za'a fara gina nasa gida, Abba so yake Muhammad ya tsaya akan abin sosai dan shi ba zai samu dama ba. Sai kuma maganar tafiyar da Abba da Mama zasu yi Abudabi nan da next week dan su huta saboda sun sha hidima kwana biyu sun gaji. Haidar ya fara tsokanar su cewa da shi zasu yafi, wai a hannun wa suka barshi? Tunda Muhammad da Mufida suna gidajensu. Har yana cewa wai honeymoon su Mama zasu tafi. Mama ta rankwashe shi akai "ka koma gidan su Baffa idan ba zaka zauna anan ba" ya girgiza kai yana kallon Muhammad "ni na san inda zanje" Muhammad ya bude ido "kar kace gida na. Bani da space" Abba yayi dariya "kaji fa Haidar. Wato wasa tare ci banban. Yar shinkafar da zasu sammaka a gidan su ita ce zai yi maka rowa" Haidar ya kai lomar abinci yace "kuma ni ba ma cin abinci ne dani sosai ba. Dan kadan ya ishe ni" Mama tayi dariya "wa yaga rijiya gaba dubu. Ai ina bayan Gidado, a cikin sati sai ka talauta su. Duk kayan garar nan sai ka cinye tas" Haidar ya bata rai "dama ai na san matsayina a gurin Mama, dadin ta ma Abba yati so na" Muhammad yace "a'a, Abba yafi son Mufida", Dariya suka cigaba da yi suna hirar su, a karshe dai bayan Haidar yayi kamun kafa da Mama sai aka yarda cewa zai je gidan Muhammad din, Sai bayan sallar isha sannan Muhammad ya samu ya zame daga gurin family dinsa ya dauki hanyar gida, ya kira number din Safiyya yafi sau adadin da zai tuna amma taki dauka, babu irin abinda baya saka wa a ransa, zuciyar sa kuma tana gaya masa cewa tana can tana kuka tana tunanin ya tafi gurin Safina ne. Ai kuwa abinda ya tarar kenan sanda ya shiga gidan ya kuma wuce directly har bedroom dinta. Tana zaune akan gadon ta ta juyawa kofa baya ta kifa kanta akan cinyoyin ta. Ya tsaya a bakin kofa yana kallon ta, ya san tana da kishi sosai, shi kuma kishin nata burgeshi yake yi most of the times, yana kara tabbatar masa da soyayyar ta a gare shi, amma kuma baya son wannan kukan. Ya danyi gyaran murya sai ta dago kai da sauri ta juyo ta kalle shi. Ya ga relief a fuskar ta sosai. Amma kuma sai ta sake juya fuska ta daina kallon sa, jan aji, ajin Safiyya yana daga cikin abinda yake kara masa sonta a kullum, Ya karasa gabanta ya tsaya yana kallon ta da murmushi a fuskar sa, idanun ta har sun kumbura saboda kuka, yanzun ma kuma hawayen ne yake kara bin fuskarsa Wani abu da Safiyya take kara burgeshi da shi shine tun da suke bata taba yi masa maganar Safina ba tun zaman da suka yi suka yi maganganu, duk kuwa da cewa ta san tana da power akan sa, tana da power din da in ta matsa zai iya sakin Safinan ko da kuwa bai yi niyya ba. Musamman yanzu da yake kara susucewa akan ta. Ya san da ace table din a juye yake, da ace Safina ce take da power din Safiyya, da baya jin zasu yi kwana daya a matsayin kishiyoyi. "Piyyyya" ya kira sunanta da wani yanayi "wai kukan menene kuma haka. Kin san yadda hawayen ki suke yin zafi a cikin zuciya ta kuwa?" Ya durkusa a gabanta yana kokarin kallon cikin idon ta. Ta sake dauke kai gefe "ni ka rabu da ni" ta fada cikin shagwaba, "Ni ba zan rabu da ke ba" ya fada yana kwaikwayon ta. Ta watsa masa harara da kumburarrun idanunta, Yayi dariya sannan ya zauna a gefen gadon a kusa da ita yana kokarin rike hannun ta, ta hana shi tana kokarin tashi tsaye still hawaye yana bin fuskarta. "Wait Babe… Ki tsaya muyi magana mana, Ki tsaya inyi miki bayani, ki tsaya in gaya miki abinda ya faru a can din da naje" ta juyo a fusace cikin kuka "bana son jin abinda ya faru a can. Bana son jin abinda kuka yi a can" sal abin ya bashi dariya. Ga mamakin sa sai gani yayi ta dawo kansa ta tura shi baya da karfi ya fada kan gadon a rigingine, ta kama kokawa da tazugen wandon sa "abinda ya faru a can shi zai faru anan ma. Ni ma ai zan iya. Duk abinda tayi maka nima zan iya yi maka" dariyar yake yi sosai yana kokarin rike wandonsa amma sai da ta cire masa ta zare shi daga jikinsa ta bar shi da gajeren wando, sai kuma ta haye kan cinyoyin sa ta zauna sannan ta fara kokawar cire tata rigar "nima ina da shi ai, duk abinda take da shi ina da shi. Kuma zan iya. Zan koya nima' ta cire shirt din jikinta ta jefar, ta bar jikinta daga ita sai lacy brar da ta kan saka idan zata yi bacci. Shi dai dariya yake yi "wait Piya, what are doing ne wai? Ki tsaya in gaya miki abinda ya far" ta jawo hannayen sa ta dora su akan kirjinta "abinda ya faru a can shi zai faru anan ma" ya dan rage dariyar sa tare da kokarin mikewa zaune, sai kuma sauran dariyar ta tsaya a kirjinsa ganin her almost naked flesh a kusa da fuskar sa, she looked very breathtaking with gashinta a hargitse ya sauko gefen fuskarta, idanunta a kumbure, fuskarta tayi ja, bata damu da kalion da yake mata ba ta fara balle buttons din rigarsa sai kuma ta fara jan rigar da niyyar cirewa, ya rike hannunta yana kokarin saisaita numfashin sa da emotions dinsa, still da sauran dariya a muryar sa "ki bari mana Babe. Nothing happened na rantse miki" "ban yarda ba" ta fada tana cigaba da jan rigar tasa daga kasansa amma ta kasa "Allah ban yarda ba" ganin ba zata tsaya ta saurare shi ba sai ya kamo fuskarta da hannu daya ya hade bakin su. Hannayen ta da ta daga da niyyar cigaba da jan rigar su ta sauke a hankali akan kafadarsa tare da zagaye kafadar da su tana kara jawo shi jikinta tare da sauke ajiyar zuciya. Ya danyi murmushi a ransa, ita ce mai ce masa wai shi ya fiya son kiss amma kuma a cikin kwanakin da suka fara learning the art of kiss ya fahimci tana so ita ma sosai, kawai dai tana jan aji ne shi yasa bata fada. Sai da ya tabbatar ya dawo da nutsuwar ta gare ta sannan ya raba bakin sa da nata, yabi lips din nata da kallo yana ganin yadida suka kara yin ja sannan suka kara zama fresh, baya gajiya da kallon su kamar yadda a yanzu yake kara tabbatar wa da kansa cewa baya gajiya da tasting din su,. Ya daga idanunsa a hankali ya sauke su akan nata da har lokacin suke a lumshe, ta bude su a hankali a cikin nasa, sun jima suna kallon juna sannan yace "nothing like this happened between me and her. Nothing like this ever happened between me and her. I couldn't do it, because I love you, and because she is related to you" a idonta ya ga alamar ta yarda da abinda yace, duk da dai akwai alamar tambaya, ya san kuma tambayar dan haka ya bata amsa "she put desire pills in my tea kettle one night, that was how she got pregnant, ba wai da son raina ba ne ba" ya cigaba da kallon cikin idanuwanta, ya ga relief sosai, more than yadda ma yayi tunani, ya fahimci abin have been weighing on her mind kawai dai soyayyar sa ce ta danne komai. Sai kuma ta rungume shi da sauri tare da kife fuskar ta a kan kafadar sa, ya saka hannun sa daya yana shafa gashin kanta dayan kuma yana shafa naked bayan ta down to the rim of her skirt. "I love you" ta fada a hankali da karyayyiyar murya, "I love you so much" ta kara fada da muryar daya tabbatar tare da hawaye ta fito, Ya danyi murmushi tare da lumshe ido yana Jin kamar zuciyar sa tana kumbura a kirjinsa da soyayyar ta, "I love you too" ya tada a hankali. Sun dan jima a haka sannan a hankali ya fada mata cikin kunnen ta "I divorce her" yaji ta rike numfashin amma bata dago ba, ya kara maimaita mata "I divorce her. Na sake ta. That was what happened da na fita. Abinda naje nayi kenan" ta dago kai daga kafadar sa tana kallon sa da budaddun idanunta, ya saka hannu yana kara gyara gashin ta da ya yi framing fuskarta. "I am no longer married to her",. Still ta cigaba da kalion sa bata ce komai ba. Ya saka hannu ya rike habarta yace "now smile". Ai kam a take murmushi ya bayyana a fuskar ta, sai taji kunya kuma ta kara cusa fuskar ta a kasan wuyansa, dariya yayi itama sai tayi dariyar sannan ya jata suka yi baya suka fada kan gadon shi yana kasa ita tana kwance akan kirjinsa. Ya mintsini gefen cikin ta, ta fara kokarin zame wa sai ya kara rike ta "Babe ko kunya babu? Babu dan kawaicin nan ma shine kike dariya ko?" Ta juyo tana kallon sa fuskarta dauke da annuri, duk tarin damuwar da ya gani a tare da ita sanda ya shigo ta gushe, ta juya idonta "ba zanyi alkunyar ba, Is it a crime dan bana son raba mijina da kowa? Musamman da wadda nake kalla a matsayin yayata? I Wish her well, duk kuwa da abubuwan da tayi min bani da nufin sharri a gare ta, ina yi mata fatan alkhairi, ina yi mata fatan samun miji na gari wanda zai so ta ya kula da ita, but not my husband. Not at the expense of my own happiness" Yayi murmushi yana shafa fuskarta, tare da jin cewa ita matar rufin asiri ce, matar da zata iya danne damuwarta dan farin cikin mijinta. Amma shi baya fatan saka ta damuwar ko da nan gaba ne. Ta shagalta da kallon sa bata san sanda ya saka hannu ta bayanta ya balle hook din brar da take a jikin ta ba. Ta danyi kara tare da zaro ido tana kallon sa, yayi juyi ya mayar da ita kasa sannan ya tashi tsaye yana karasa cire rigar da ta fara cire masa "let's finish what you started. Dama kince kin iya ko?" Ta fara girgiza kanta tana dariya "ni ba haka nace ba, baka ji dai dai ba" ya cije lips dinsa yana jan skirt din jikinta irin yadda tayi masa "naji komai, har da cire min wando ko? In ma banji ba yanzu zaki maimaita min inji" ta mike zaune da sauri tana kokarin rike skirt dinta, hakan ya bayyanar da kirjinta sai ta koma ta kwanta da sauri tana rufe kirjin da hannayen ta tana dariya sosai "ka bari...…. Allah ka bari ......" Bai bari ba sai da ya zare skirt din yayi jifa da shi irin yadda tayi wa wandonsa. Lacy pant dinta ya bayyana dan uwan brar, ta kifa da sauri ta koma rub da ciki a kokarin ta na boye jikinta, tana dariya tana bubbuga kafafuwan ta a kan gadon "Dan Allah ka bari Yay Muhammad". Bai bari ba, dan abinda ya gani ba zai barshi ya bari din ba, He thought her some lessons, kamar yadda shima ya koyi wadansu daga gare ta. Kamar dazu da safe, sun yi yawo sosai tare da junan su a sararin samaniya, kuma kamar dazun, bata gayyace shi zuwa duniyar ma'aurata ba shima kuma bai matsa mata ba duk kuwa da matsuwar da yay da son kai ziyara can din. Sai dai ya fahimci wani abu, kusan kashi saba'in na tsoron abin da take ji ya ragu. Sai da suka tsarkake jikin su har ta saka kayan baccin ta sannan ya jefa mata hijab dinta, ta juyo tana kallon sa ta ga jallabiya ce a jikinsa da dogon wando, "gurin Daddy zamu je" tayi sauri ta kalli agogo, 15 minutes after 9, tunda taga isha tayi ba su je ba sai ta saka a ranta cewa yau ba zasu je ba, Ya daga kafada "munyi alkawarin zuwa kullum. Maybe ma yana can ya kasa kwanciya yana saka ran zuwan mu", Cikin murna ta saka hijab din akan kayan baccin ta suka tafi. Yana daga cikin abinda yake kara mata son Muhammad, yadda yake damuwa da duk abinda ya shafe ta. Da yake dare ne babu traffic dan haka basu jima ba suka je. A zaune kuwa suka tarar da shi akan kujerar sa, har kayan bacci an saka masa amma bai kwanta ba, idonsa akan hanya. Tana shiga murmushi ya bayyana akan tuskarsa ya mika mata hannu, ta karasa da sauri ta rike hannunsa sannan tayi kissing cheeks dinsa "daddyna" ta fada cikin shagwaba. Muhammad ya cigaba da tsaiwa a bakin kofa yana kallon su, fuskarsa dauke da murmushi….... Daddy ne da kansa ya ce mata kar ta shiga cikin gidan a ranar ta bari sai gobe tukunna, maganar da Muhammad ya gaya mata dazu ya saka ta fahimci Safina tana ciki kuma Daddy baya son su hadu a yanzu. Kafin ta fita dai daga gidan taga twins, su suka raka su har mota sannan suka gaya mata maganar da ta saka ta farin ciki "Yaya Mustapha ya dawo dazu. Daddy ne ya dawo dashi, Yanzu ma yana dakin sa yana gyara kayansa". Amma basu yi mata maganar Safina ba kamar yadda ita ma bata yi musu ba. Her🧕🏻 Washegari da safe na tashi ina jin zuciya ta fara kal, haka kawai nake jina cikin nishadi, Ranar da wuri na tashi ban yi dogon baccin da na saba yi kwanan nan ba. Muhammad tun da ya fita da assuba bai dawo dakin ba da na kira shi a waya sai yace min yana gym. Ban sani ba ko rashin jin dumin jikin sa a tare da nine ya saka na kasa baccin? Na dauko waya ta na tura wa mutane message din godiya da ban gajiyar biki. Wadansu kuma na kira su, musamman kawayena da suka zo daga nesa, na kira matar Abdul ita ma, ita ce take gaya min cewa washegari zasu koma Berlin, Amma sai na kasa kiran Aunty Hajjo, sai na tura mata message kawai, Na kira Mommy itama, muka gaísa sai take ce min zata je Katsina, ban tambaye ta me zata je yi ba sai nayi mata fatan alkhairi tare da tambayar ta ko tana bukatar wan abu, bata nuna min tana bukatar komai ba amma muna gama wayar na tura mata kudi. On impulse sai na tura wa Mustapha message shima nace masa job offer dinsa tana nan a duk lokacin da yake bukatar ta, Ba'a jima ba yayi min reply "zan je Katsina, in na dawo we will talk about it" nay murmushi kawal Sai kuma na kira Hajiya, anan muka jima muna hira har kyalkyala dariya nake yi, tana ta tsokana ta wai aure ya saka murya ta ta kara zaki, wai ko sukari mijin yake bani ina sha kullum,. Sai kuma ta sake yi min doguwar nasiha akan zaman gidan miji, kula da mijin da yan'uwansa da kuma kula da addini, ta kuma gaya min xewa Mommy ta gaya mata abinda ya faru da Safina, sai ta ja kunne na "babu ruwanki. Tsakanin ki da mijinki daban tsakanin ki da su Sa'adatu daban. Kar ki tofa albarkacin bakin ki. Kiyi ta addu'a Allah ya daidaita lamarin" ta bani shawarwari masu kyau kuma na saka a raina cewa zan dauka. A karshe nace mata "Hajiya ina ma zaki yarda ki dawo gidan nan. Tunda can din da kike babu kowa sai ke kada'" tayi murmushi tace "ban taba zama ni kadai ba Fiyya. Yara uku ne yanzu haka a gaba na. A hakan ma na gode da kulawar ki gare ni. Kawai dai ki ringa zagayowa lokaci zuwa lokaci muna gaisawa. Kuma duk abinda kike bukata ki kira ni ki gaya min baki da shamaki", nayi mata godiya sai kuma na tuna da zancen yan akin da nake so dan haka nayi mata, na gaya mata guda biyu ko uku nake so masu hankali, sai kuma maza guda biyu, tace min mazan in yiwa Muhammad magana shi ya kamata ya samo mana, idan kuma ace ta samo shikenan already akwai wasu da 2tace min nan da next week za’a kawo minkwararrun da zasu yi keeping min gida spotlessly clean, Har nayi niyyar kiran Umma sal na fasa, na dau tura wa Salima message tare da sauran kawayena. Daga haka na tashi na gyara dakin Muhammad tas na kunna turaren wuta na gyara toilet din shima, sai na koma nawa dakin na gyara shi shima na saka turaren wuta tare da different varieties of room fresheners sannan na shiga toilet nayi wanka na fito na shafa mai ina lura da yadda fata ta take kara wani sheki na musamman da ba zan tya cewa ko na menene ba, na saka wata doguwar rigar da aka dinka min da atampa amma tsahonta da kadan ya wuce guiwa ta, ta kuma bude sosai daga waist, armless ce bata da hannu sai kafada kawai. Na gyara fuska ta nayi kwalliya mai kyau, sai nay packing gashina a tsakiyar kaina da dankwalin atampar na barshi ya sauko zuwa wuya. Na feshe jiki na da turare sosai sannan na fito daga dakin na sauka zuwa first floor, na shiga gym din Muhammad na tarar da shi yana kokarin fitowa, kida yana tashi kadan kadan a cikin gurin. Na tsaya ina kallon sa cikin fararen track suit masu black strips. Yayi min murmushi yana bina da kallon appreciation yace "you look like a Barbie" na danyi juyi a gabansa tare da bowing irin gaisuwar turawan ingila nace "good morning" ya karaso inda nake yana goge fuskar sa da hanky yace "Baby..... Good morning Baby zaki ce" na juya ido na "naki din" ya langwabe kai "Please" sai na lakuce masa hanci na wuce shi ina dudduba kayan wajen. Ya biyo ni a baya "wanne zaki fara using?" Na bude ido "Allah ya tsayi gatari da saran shuka, so kake inyi irin wannan?" Na fada ina nuna arms din sa da suke a mummurde, yayi murmushi "no, you will not. In dai har ba extreme kike ba. In dai ba lifting weights kike yi ba ba zaki yi muscles ba, kawai treadmill zaki ke hawa, zai kara miki lafiya ya cire miki kasala, ya yi improving mood din ki, ya saka ki bacci mai dadi, ya......" Na saka hannu na rufe masa baki "thank you coach, but I am not interested" ya dan ciji hannun nawa nayi sauri na cire "ouch" sai ya matso ya rungume ni ta baya ya rada min a kunne na "zai kuma hana ki yin kiba" na dago kai ina kallon sa sai ya kashe min ido, ya san lago na, tun a makaranta ya san bana son kiba amma kuma ina son cin abinci, na juyo ina fuskarta sa nace "okay you win. Zan ke zuwa ones a week" yace "three times a week" nace "two times a week" yace "deal, Now let's start" nayi sauri na zame nayi gaba "ba yau ba fa. Sai dai gobe" ya biyo ni ya jawo ni jikin sa yana shanshana gashin kaina "hmmm. ba ki da gaskiya. Guduwa zaki yi ko?" Na juyo ina kallon sa sai ya mayar da fuskarsa wuyana "hmmm. Kamshin ki dad" na ture shi ina dariya "ka tafi ka je kayi wanka" ya sake jawo ni yana langwabe kai "ki zo kiyi min" na bude ido "ka ga girman ka kuwa?" Yace "sai in sunkuya" na bude hannu na "a nawa zan yi maka wankan?" Ya kama hannun tare da kissing tsakiyar tafin hannun Yace "anything. Zan biya price mai kyau". Na kama hannunsa "okay. Muje in yi maka" muna fita na saki hannun na tafi a guje na shige kitchen na rufe kofa. Ina jin sa yana dariya sannan naji ya hau sama. Na dan jima ina kallon kitchen din nawa ina jin dadi a raina. Na shafa worktop din tare da deciding cewa ranar zan fara girki a gidan. Sai dai ban san yadda zan gayawa Mama cewa ta daina aiki mana da abinci ba. Na san haka alama ce ta soyayya amma nima ina son in fara girki a gida na Na fita na tafi dinning, already kuwa har an kawo abincin Esther ta gyara gurin ta jera, na bude sai na ga kosai, naji dadi sosai dan na dade ban ci kosal ba. Sai kunun madara da akayi thickening da plumbs, Daga nan kuma sai farfesun kayan ciki, ina bude shi naji kamshi mai dadi sai nayi deciding zan ci, dan ni in ba ni nayi farfesun kayan ciki ba bana iya ci amma wannan zan ci. Na ga Esther kuma tai mana nan bread din da zaiyi going well with the pepper soup. Komawa nayi kitchen na dafa mana tea, nazo na zauna na cigaba da replying congratulatory messages din da ban samu damar budewa ba har Muhammad ya gama ya fito, muka ci abincin tare ina mamakin yadda ya ci kosan sosa dan ban taba tunanin yana ci ba, sai kuma na fara tsokanar sa da cewa dan fillo ne shi. Nayi masa maganar ko zai gayawa Mama ta huta da yi mana girki haka sai yace babu ruwansa sai dai ni in gaya mata, sai na bar maganar nima, Amma a raina nayi deciding abinda zanyi, Ranar ma a gida muka wuni. Sai magrib muka fita muka je gaishe da Daddy, Na tarar Mommy da Mustapha da Safina sun tafi Katsina, sal twins ne a tare da Daddy, Naji kamar in zauna sal ya gaya min washegari zasu dawo, kwana daya suka ce zasu yi, In almost total silence muka koma gida, ban san me yasa muka yi shiru din ba bayan kuma shiru shine last thing da mu kan yi idan muna tare, haka yayi driving da hannu daya, hannun sa dayan rike da nawa, ki da yana tashi kasa kasa a motar. And I found myself thinking "why not tonight?" Amma kuma zuciyata tana karkarwa with the thought, Haka muka je gida, haka kuma muka shiga ciki muka hau har second floor, in silence but hand in hand. Sai da muka gama hawa muka tsaya a dan corridor din da ya raba dakin sa da dakuna na sannan ya juyi da ni yana kallon cikin ido na yace "you will come, right?" Na dan gyada kai na kadan amma ban kalle shi ba sai ya yi kissing hannuna yace "I will wait" sannan ya juya ya tafi dakin sa. Nawa dakin na shiga na ciye kayan jikina na shiga toilet nayi wanka tare da duk sauran shirye-shiryen bacci, na fito nayi sallar, asking God for courage and strength din da na san bani da su sannan na rufe dakina na tafi na sa. A kwance na tarar da shi a kan gado sanye da kayan bacci, ya kashe fitila except for the bedside lamp din da ta haska min shi. Na cigaba da tafiya a hankali wat zuciyar already tana gaya min in juya in koma dakina in rufe kofa, Amma ban biye mata ba sai na je na zauna a gefen sa kafafuwa na a kasa ina kalion sa. Na fahimci ba bacci yake yi ba, idon sa biyu, amma bai bude idon ba ya cigaba da kwanciya a haka. Na saka hannu na na dama a hankali na shafa sumar kansa ina jin laushin ta a hannu na idanuna akan fuskarsa, fuskarsa doguwa ce amma ba sosai ba, tana da dan fadi kadan, wanda ya kara mata cika da kwarjini. Na jawo hannun da ga cikin gashin kan zuwa sajen da ya zagaye ya kuma kawata fuskar, a hankali ya bude idanunsa ya sauke su a kaina. Muka cigaba da kallon juna through the dim light of the coloured bedside lamp. Na matso da fuskata dai dai ta sa sannan na lumshe ido na na dora lips dina akan nasa a hankali kamar mai tsoron ta ba wuta. it started lightly kamar an kunna ashana, and then grow like a wildfire da ta fara cin bodies din mu baki daya. Hannu daya ya saka ya daga ni ya hawo dani kan gadon sosai sannan ya juye ya mayar da ni zuwa ¡kasan sa. Sanda na kara sanin inda nake a lokacin na fahimci na rasa kayan jikina. lokacin da ya raba jikin sa da nawa na some seconds, da ya dawo sai na fahimci ya rasa shima nasa kayan. A lokacin ne kuma fear din ta dawo, the memory of that night, the pain, the fear, the….... Na fara ture shi cikin kuka. "No. ..... Stop..... Dan Allah....... Please........." Gabakidaya jiki na karkarwa yake yi. Farko kamar bai ji me nake cewa na, daga baya kuma sai ya sake ni sannan ya kwanta a gurin yayi shiru yayin da ni kuma na ja jikina zuwa karshen gado na takure ina karkarwa tare da sheshshekar kuka. Mun dan jima a haka sai ya mike zaune sannan ya fara kokarin tashi. Sai dai yanayin sa ya taba zuciya ta sosai, fuskarsa ta nuna zuciyar sa tana cikin damuwa and that was something da tawa zuciyar ba zata iya dauka ba. Na saka hannun dama na na riko na hagunsa, ya juyo muka hada do through the dim light, a take aka samu magana aka kuma samu fahimtar juna a tsakanin zuciyoyin mu. Ya sarkafe yan yatsunsa cikin nawa, na kuwa rike su kam kam trying to draw strength from him. A hankali ya juyo ya dawo position din sa, still idanuwan mu a cikin na juna, ya kama ¡hannuna na hagu a cikin na daman sa yayi kasa dasu a tare zuwa ga abinda nake tsoron, na kankame jiki na tare da rintse idona a lokacin da naji yana karanto addu'ar saduwa da iyali. I waited feverishly for the pain. It came, but just a little. But then something came too. Something that took us away from this world and into another. A world that we never knew existed before. Duniyar da mu biyu ne kadai a cikin ta, mu biyu, jiki biyu, ruhi biyu, zuciya biyu but all merged together as one. Maman Maama✍🏻[07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Seventy : One Family A cikin kai na naji karar alarm dina na sallar asuba, na dan bide idona cikin nauyin bacci tare da jawo wayar na saka alarm din a snooze, sai kuma kwakwalwa ta ta tuna min cewa wannan shine second snooze da na saka wa alarm din dan haka na tabbatar daga ni har Muhammad muna gab da makara sallar asuba. Daga nesa ina jin ana ta kiraye kirayen sallah. Na danyi murmushi ina jin saukar numfashin Muhammad a bayan wuyana, hannayen sa a zagaye a cikina, kafafuwan sa a sarkafe da nawa. Na lumshe ido na bude ina kokarin rage nauyin baccin da yake ido na tun kafin ya ci karfina. Idan ban da kiran Allah na san babu abinda zai tashe ni daga wanna kwanciyar. Sam daren jiya Muhammad bai bar idona ya rintsa ba, kamar yadda bai bar jikina ya huta ba. Sai da ya karar da dukkan karfin da yake jikina sannan ya rabu da ni to have just few hours of sleep. Shima kuma gashi nan ai zai makara masallaci. Na mika hannu na kuna bedside lamp din da take bangare na. Na yi juyi ina jin yadda jikina gabakidaya yake amsawa, musamman kafafuwana da nake jin su kamar ba nawa ba. Na sauke nauyayyun idanuna akan fuskar Muhammad da yake bacci, ya dan motsa yana kokarin sake jawo ni jikinsa. Na shafa fuskar sa, a hankali nace "assalatu khairun minal bacci" ya dan motsa idon sa kadan, na shafa kunnen sa tare da jan fatar kunnen "ka tashi fa. Ana can ana samiallahu liman hamidan a masallaci" ya dan bude idanunsa da suke cike da bacci yana kallona, and then his face lit up with a smile "hey Babe" ya fada yana kara jawo ni jikin sa, "sallah" na fada ina yanje fuskata tare da kare bakina da hannu na. Ya cire hannun nawa tare da saka fuskarsa a cikin wuyana yace "bacci" nace "kaje kayi sallah sai kazo kayi" ya dago kai yana min wanna kalion na sa yace "inyi ko? Okay, bara inyi sallar you will get your wish" na bude ido "bacci fa nake nufi, kayi bacci nake nufi. Kai kace bacci bai ishe ka ba" ya janye jikin sa tare da sauka daga kan gadon ganin cewa da gaske zai makara masallacin "kar ki chanja magana yarinya. Zan je in dawo. Zan zo kuma inyi din kamar yadda kika ce". Da sauri ya shiga toilet, bai jima sosai ba ya fito da jallabiya, ya kunna min fitilal dakin cikin tsokana ya juyo yayi min qwalo ni kuma na harare shi a dai-dai lokacin da aka fara tayar da ikama a masallacin da yake zuwa ya juya da sauri ya fita ni kuma ina yi masa dariya. Sai da ya fita sannan na yaye abun rufata tare da kalion rigar baccin Muhammad da take jiki na ina murmushi. Na tuna jiya da daddare da ya boye nawa a kasan gado sanda nake kokarin zuwa toilet dan gyara jiina yace wai shi bai gansu ba, ko a tunanin sa zan tashi a haka in shiga toilet din ne oho? Nayi nayi ya shiga toilet ya dauko min ko da bathrobe ce amma yaki, a karshe sai na yaye bedsheet din kan gadon na nannadashi a jiki na na tashi yana ta min dariya, ai kuwa ina tashi na tafi zan fadi saboda kafafuwana da naji babu karfi ko kadan a jikin su, sai dauka na yayi da sunan zai taimaka min amma ashe taimakon na mugunta ne, a karshe sai da ya cire min bedsheet din, wankan ma kuma bai barni nayi sa cikin salama ba sai da ya kara min wani dalilin yin wankan. Na mike tsaye a gaban gadon ina dan bubbuga kafafuna a kasa ko zan samu inji sun dawo dai dai, nayi kwafa a raina, duk kokari na na ganin nayi wanka cikin daren dan kar inyi da assuba amma yanzun ma sal nayi wani, takanas yaje kitchen ya hado min abinci cikin daren bayan munyi wanka ya kawo min har kan gado wai dan in dan samu karfin da nayi masa complain ya karar min, ashe kan sa yake yi wa tanadin karfin, dan abincin ko gama digesting bai yi ba ya sake tara min wata gajiyar. Jin ana kokarin idar da sallah a masallaci ya sa nayi saurin shiga toilet nayi wanka sannan na goge jikina na daure gashina a cikin karamin towel na saka riga da hijab din da na ajiye a dakin sa domin sallah na tayar da sallah. Ina cikin yin sallar ya shigo, ina jin sa yana gyara gadon har na idar sannan ya zo kashe fitila ya kuma rufe blinds din windows sannan ya kwanta, Sai da nayi azkar dina na gama sannan na cire hijab din na karasa drying gashina da towel din sannan na tafi na kashe bedside lamp na kwanta nima, a tunani na saboda dadewar da yayi a kwance da kuma baccin da na san yana ji, yayi bacci, sai dai ina kwanciya ya jawo ni "me kika ce da zan fita? In dawo inyi ko?" Na danyi dariya tare da juyawa ina fuskantar sa "ka san abinda nake nufi ai. Kawai kana son ka juya min magana ne" ya fara kissing wuyana "say whatever you want to say. Ni dal abinda naji shi nake amtani da shi" na dago kansa ina kokarin kallon fuskar sa cikin duhun da yake dakin "hey! Are you not tired?" Ya danyi dariya "menene tired? lam just getting started". Na danyi murmushi tare da kara shigewa jikinsa kamar zan shige cikin jikin nace "ni dai bacci zanyi, Allah kuma kar ka tashe ni daga bacci na" ya danyi dariya tare da gyara kwanciyar sa ya dora ni a jikinsa yana shafa bayana ta cikin rigar jikina yace "Okay, let sleep. Only dan kar kiji toro ki hada kaya ki gudu", Na danyi murmushi tare da kara narkewa a jikin sa ina kokarin komawa bacci, Hancina yana shakar kamshin jikinsa, kunnuwana sun sauraren bugun zuciyar sa, jikina yana exchanging dumi da nasa jikin, ga hannun sa yana shafa bayana, sai naji kamar ban taba jin comport irin wannan ba. Bacci ya fara daukana kenan naji muryarsa, "Hey Babe!" Cikin bacci nace "uhmm?" yace "you know I love you, right?" Na gyada kai na a kirjinsa nace "I know" yace "good. And now I want to update you on the love. Ya karu, ya kara girman da nake jin har ban san inda zan saka shi ba dan ya cika zuciyar gabakidayan ta, har yabi jini ya zagaye dukkan organs na jiki na. Yanzu ba zuciyar kike controlling kadai ba, gabaki daya jikin naki ne. And I also want you to know that these days da muke tare are the best days of my life, I will never forget yesterday's night. I enjoyed every second of every minute of it". Na dan daga fuska ta nayi kissing adam's apple dinsa "I love you too Baby. Ban san yadda kake jin so na a zuciyar ka ba, amma ni na san yadda nake jin naka, Na kuma tabbatar yafi nawa girma, da ace zan iya fito maka da shi ka gani na san kai ma da zaka yarda da hakan. But ba zan iya yin hakan ba, amma nayi alkawarin cigaba da nuna maka ina son ka every second of every minute of my life. Forever and ever" na mayar da kaina na kwantar a kirjinsa sannan nace a hankali ina shafa gashin kirjinsa "and I also enjoyed the night" ya danyi dariya tare da kara rungume ni yana cewa "na gaya miki this is only the beginning, enjoyment yana gaba idan mun iya, yanzu koya mu ke yi". Ranar sai alarm din sallar azahar ne ya tashe mu. Da sauri yayi alwala ya fita masallaci ni kuma na tashi na gyara dakin sa kamar yadda nake yi kullum duk kuwa da cewa da gaske jikina yana yi min ciwo, sal da na tabbatar ko ina kamshi yake yi a dakin sa sannan a koma nawa dakin na hada ruwa mai zafi sosai a bathtub na zuba sinadaran rage ciwon jiki da na kamshi sannan na shiga na kwanta na dauki waya ta nayi ta replying messages tare da scrolling through social media, a lokacin ne naga reply din Salima, a Maganar ta na fahimci wanna karon ma iyayen nasu sun boye musu abinda ya faru, ta dai gaya min cewa Umma bata da lafiya hawan jinin ta ya tashi tana asibiti amma da sauki, sai kuma tace min zasu zo ita da Salim very soon, har da cewa in ajiye musu kazar amarci. Sai kuma na ga message da ga Safina, bana son abinda zai bata min rai dan haka ban ma bude ba nayi deleting na kuma yi blocking dinta, ina fatan wata rana abubuwa su daidaita a tsakanin mu ko dan Mommy da twins, amma na san ba yanzu ba. Tunanin Mommy ya sa na kira ta a waya, na gaishe ta sai ta ce min suna airport yanzu zasu baro Katsina ita da Mustapha, har Mustapha ya ce ta bani wayar, muka gaisa ya tambaye ni ina ango na, nayi murmushi kawai ban ce komai ba sai yace zai shigo gobe "zan zo in ba shi amanar kanwata, kin san na gaya miki zan fasa bakin duk wanda ya taba min ke ko?" Nan ma murmushi kawai nayi sannan nayi musu fatan zuwa gida lafiya, Da yake tub din mai keeping temperature din ruwa ne han haka har a gama abinda nake yi ruwan bai huce ba, sannan nayi wanka da sabulun wanka na mai kamshi na fito. Riga da skirt na saka designers masu dan banzan kyau, rigar da kyar take rufe cibiyata da nayi motsi kuma sai ta fito. Skirt din kuma irin yadin nan ne mai rawa a duk sanda mutum ya motsa, na gyara gashina na shafa masa mai nayi drying dinsa sosai ina tunanin dole in je inyi kitso tun kafin Muhammad ya saka gashina ya lalace saboda yawan wankewa. Sai kuma na dora hijab akan kayan nayi sallah, amma da na idar sai na kasa cire hijab din dan ina jin kunyar kayan jikina. Kamar yadda nayi tunani a dinning na same shi yana jira na yana waya, ina shigowa yayi min alamar "what?" Da hannun sa, na daga kafada nima alamar tambaya sai ya nuna min hijab din jikina, na tura baki kawai na jawo warmers din Mama na fara zuba mana faten irish din da tayi mana wanda ya sha dagargajajjiyan naman kaza, a hankali ya janye wayar da ga bakin sa ya kare mic din sannan yace "ba ki da gaskiya" na harare shi "ina da gaskiya ta, haka kawai mutum ba zai saka hijab ba sai a ce bashi da gaskiya?" Ya cigaba da wayarsa ni kuma na fara hada masa tea na tura masa gabansa na fara hada nawa. Na fahimci da Mutida suke wayar sai naji ina sha'awar closeness din su, sai hirar su suke yi suna dariya, sai da ya fara saka ni a cikin maganar sannan tace ya bani, na karba nima na tsokane ta akan zaman gwaurancin da take yi, tace ai yanzu ma shiri take yi zata je gidan Mama ta sake yin kwana biyu kafin su maman suyi tafiya, kafin nan kuma take saka ran mijin ta zai dawo. Sai kuma ta tambaye ni wai menene sirrin? Wai rabon da taji yayanta cikin wannan nishadin tun kafin waccan rabuwar ta mu. Nace in tana son sanin sirrin ta zo gidana zan gaya mata. Muka yi sallama. Na ajiye wayar ina jin idon Muhammad a kaina. "Zaki cire ko sai nazo na cire miki?" Na juya ido na tare da zuba syrup akan pancakes din da Esther ta hada mana. Ya jawo ni na fado kan cinyarsa yana kokarin saka kansa a wuyana sai kuma hijab din ya tare, ya daga ni ya zare hijab din, "na biya sadaki fa, ko baki sani ba?" Nayi sauri na koma na zauna akan cinyar sa tare da boye jikina a jikinsa "ni ban sani ba…….. Yaushe ka biya?" Ya dago ni daga jikin sa na sake komawa tare da cusa kai na a wuyansa, ya saka hannunsa yana shafa fatar cikina yace "na gaya miki baki da gaskiya, Ga kuma toro" na dago tare da hararar sa "tsoron wa zanji? Ba dai kai ba ko?" Yace "in ba tsoro ba ki tashi mana in ga kwalliyar. Kika sani ko in bayar da tukuici?" Na daure duk kuwa da kunyar da nake ji din na tashi tsaye a gabansa "see? Ya ka gani?" Ya bini da kallon appreciation yace "kinyi kyau, Sosai. Na gani kuma na yaba" na juya ido na "dama dan ka yaba aka yi. Saura tukuici" na mika masa hannu, ya kama hannun ya jawo ni dab da shi sannan yayi kissing fatar cikina da ta bayyana. Na danyi flinching tare da ja da baya. Sai ya sake jawo ni na dawo kan cinyar sa, gashina da ban daure ba ya zubo akan fuskarsa, ya lumshe ido yana shakar kamshin da yake fitowa daga jiki na, ya bude idon ya bini da kallon da na riga na san ma'anar sa, gain irin kallon da yake yi min ya sa nace a hankali "abinci. Na riga na zuba. Zai huce" ya hade goshinsa da nawa, idonsa akan lips dina yace "sai a zuba wani". Sai wain kuwa aka zuba............ Sai da muka samu cin abincin sannan na tambaye shi "wai abincin me muke ci ne? Breakfast ko lunch?" Ya daga kadafa "don't know. Don't care" sai da muka gana ci sannan na gaya masa plan dina "ina son zanyi girki muje da shi gidan Abba muyi dinner a can tare da su. Maybe in nayi haka Mama zata daina wahalar yi nana abinci kullum" ya danyi shiru yana tunani sai kuma yace "good idea, She will like it. Amma zaki iya cin abinci a gaban su?" Nace "an gaya maka kowa dan fillo ne irin ka" yayi dariya "me and you, za'a banbance waye dan fillo a cikin mu yau. But let's call her mu gaya mata" ya fada yana dauko wayar sa, ya nemo number dinta ya miko min, ina daga kan cinyarsa na karba naga yadda yayi saving number din "my love" amma ban kira ba sai na dauko wayata na saka number nayi saving as "our love" ya danyi murmushi tare da kissing gefen wuyana. Nayi dialing ina lissafin yadda zanyi introducing kaina a wajenta. Tana fara ringing ta dauka da sallama, Muhammad ya kara matso da kansa yana jin abinda take cewa, na amsa sallamar sannan na gaishe ta, ta amsa da "kun tashi lafiya Safiyya?" Naji dadi, ta karbi number ta kenan. Na amsa "lafiya lau. Ya Haidar?" Ta amsa da "yana wajen aiki. How are you? Ya bakunta?" ace "alhamdulillah" sai kuma nayi shiru, ta danyi shiru itama sai kuma tace min "ina fatan babu abinda kuke bukata ko?" Nace "babu komai Mama….... Dama…..... Dama cewa nay!" Muhammad yace "Mama dama cewa tayi wal yau." Na janye wayar da ga kusa da shi tare da toshe masa baki a zare masa ido, sai kuma na tashi daga kan cinyarsa na matsa gefe nace "Mama dama cewa nayi yau kar kuyi cooking dinner. I want to cook for you. Sai inyi anan mu taho dashi mu ci tare da ku" naji murmushi a muryar ta "are you sure Safiyya? Ke da kike hutawa kin sha wahalar biki?" Na dan girgiza kai na "babu gajiya ai Mama. Na huta sosai, I just want to cook for you kafin ku tafi ance zakuyi tafiya" tace "Okay. Shikenan. Lallai yau Haidar da murna kenan. Dama yace gurin ku zai daw idan muka tafi", Muka danyi hirar Haidar kadan sai tace in bata Muhammad. Na mika masa ya karba suka dan yi magana sannan ya katse yana kallona "da me zan taya ki aikin?" Na girgiza kaina "na gode. Dan Allah ka tafi daki ko hanyar kitchen bana son ka je. Kana zuwa ba zaka barni inyi aikin ba". Esther na kira a waya nace ta zo kitchen muyi aiki. Muhammad kuma ya koma sama. Tana zuwa na gaya mata abinda zamuyi ta fara lissafi, "Zamuyi traditional dish daya. Sai muyi Arabian daya. Sannan English daya, Sai snacks.… And salad .... And pepper soup" Nayi dariya "Esther and pepper soup" tayi dariya itama. A take muka fara plans a abinda zamuyi, muka duba abinda bamu da shi muka yi ordering online sannan na tafi yin sallah na barta tana marinating nama da sauran preparations, ban biye wa Muhammad ya tsayar da ni ba dan haka ina idar da sallar la'asar na koma muka fara aiki. Babu bata lokaci muka kammala, sai da na tabbatar komai ya zama set saura finishing sai na bar mata na koma daki na na shiga wanka. Cikin sauri na fito lokacin already ana kiran sallar magrib, na shirya cikin doguwar rigar atampa wadda akayi wa simple yet classy dinki wanda bai kama min jiki ba, na saka one of my mother's pendent sannan nayi simple kwalliya na shafa turare. Lokacin Muhammad ya shigo yace min zai je masallaci, idan ya dawo zai jira ni a waje, nima sallar nayi sannan na karasa shiryawa na yafa mayafi na na fito. Already na tarar Esther har ta shirya abincin a baskets ta sauka da su kasa, mai gadi ya taya ta dauka suka zuba a motar da Muhammad ya fito da ita sannan muka tafi. Ni nayi driving, Muhammad yana zaune a gefe yana ta min labarin dramas din da akanyi a gidan su akan wanda akafi so da wanda ba'a so. Haidar ne wai kullum mai complain cewa Mama bata son shi duk kuwa da cewa shine mai sunan babanta A hakan kuma yake yaudarar ta ya saka ta tayi masa abu tunda idan bata yi ba zai ce bata son sa, Wannan kuma shi yake sa kullum suna rigima da Mufida ita kuma saboda ita kadai ce mace kuma ita ce karama. Da muka je gidan shi ya taimaka min muka fara shiga da kayan cikin gidan. Bayan mun shiga mun shiga Muhammad ya aiko aka shiga da sauran kayan. Babu kowa a parlourn, a zauna sai Muhammad yazo ya zauna kusa da ni, na dan harare shi, "ka tashi daga nan" ya daga kafada "saboda me?" Nace "ni dai ko ka tashi ko kuma ni in tashi, so kake a fito a gan mu a haka?" Yana murmushi yace "to menene? Ba su suka daura mana auren ba?" Nace "ni dai ka tashi" sai ya rada min a kunne na "ki zo muje in nuna miki dakina" na bude ido tare da girgiza kai, yace "kafin su fito mun dawo fa. Nuna miki kawai zan y" nace "kayi alkawari nuna min kawai zaka yi?" Ya miko min karamin danyatsansa "na yi alkawari" na saka nawa a ciki muka daura sai nace "a ina dakin yake?" Ya juya yana nuna min bayan mu "a can.…….." Sai kuma maganar to tsaya bai karasa ba. Na kalli inda yake nuna min sai muka hada ido da Mama, tana tsaye a hanyar da na bi ranar nan na je dakin ta da kyakkyawan murmushi a kwance akan kyakkyawar fuskarta. idanunta a akan mu. Mufida tana tsaye a bayanta. Nayi sauri na zare dan yatsa na daga cikin nasa ina rarraba ido, ya mike tsaye sannan ya durkusa ya gaishe ta nima nayi yadda naga yayi, sai dai shi da fulatanci yayi ni kuma nayi da hausa, kamar hadin baki sai ga Abba da Haidar nan sun shigo daga waje, take Abba ya fara tsokana ta wai mun wuce su a hanya ina ta gudu a mota, Mama kuma ta fara kare min wai Muhammad ne ya koya min gudu da mota. Haidar yace "yau dai finally an samu wadda Mama take karewa against Hamma" na harare shi ina so inyi masa korafin bai zo gidan mu ba tunda na tare sai kuma na kasa cewa komai, ina jin Muhammad yayi magana da fulatanci yana dariya sai Mufida tace min "wallahi gulmar ki yake yi. Wai kin gama cika baki amma muna shigowa kinyi shiru" na dago kai na harari Muhammad din shima amma still ban ce komai ba. Bai rabu da ni ba ya cigaba da tsakana ta wai kullum ina tsokanar sa wai yana da kunyar fulani, gashi nan yanzu nice na zama bafulatanar tunda na kasa yin magana ma. Na dauki waya ta na tura masa message "zan kama ka ne, wallahi zaka gane kuren ka". Daga nan sai Abba ya fara tambayar sa maganar zuwan mu Kura, Muhammad ya gaya masa cewa next weekend yake son muje lokacin munyi two weeks, da yaso muje bayan daurin aure kafin biki amma sai Daddy ya nuna yafi son sai bayan bikin tukunna. Sai Abba yace already ya samo contact din wani mutumin kura mai suna Alhaji Basiru, ya kuma yi masa maganar zuwan mu da abinda zai kawo mu, dan haka idan munje gurin sa zamu sauka shi zai yi guiding din mu har mu samu abinda muke so. Ya karasa maganar da cewa "kiyi ta addu'a kinji Safiyya? Komai ya kusa wucewa da yardar Allah". Na gyada kai na kawai ina jin kamar zanyi kuka. Na san na jima ina kuka a gaban ubangiji na ina neman mafita da kuma sakamako na alkhairi, amma yanxu da alkhairin ya zo sai nake jin cewa it is more than I have ever asked for. Mama ce tace muje mu shirya dining table ni da Mufida, sai da muka bar gurin su Abba sannan na fara magana ina kallon dan karamin cikin jikin Mufida, "ki zauna tun kafin baban baby ya zo yace na wahalar ma sa da babyn da" na karasa ina ja mata kujera a dining set din. Ta fara bude warmers din da na fara ajiye wa a saman table din "wai duk ke kika yi wannan girkin? Ke kadai?" Nace "no. Ba ni kadai bace ba. Akwai mai aiki na ta taimaka min sosaj" tace "still... Kinyi kokari sosai" nace "ina son girki ne. Bana gajiya da shi" Muka cigaba da setting table din muna hira, ita ta nuna min inda kowa yake zama sannan na saka masa abinda zai bukata. Sai dauka gama ta koma tace musu mun gama. Suna shigowa kuma sai naji na kuma takuwa, na zauna kawai Mufida ta bude abincin tana tambayar kowa abinda zai ci, Mama tayi mamaki "wai da yawa kika yi abincin Safiyya" nace "babu yawa sosai Mama. Kawai dai ban san wanda zaku fi so ba shi yasa nayi varieties". Abba tuwon da nayi na markadaddiyar shinkafa da miyar danyar kubewa yace a zuba masa, yana fara ci yace a dibar masa wanda za'a dumama masa da safe dan kar Haidar ya cinye. Naji dadin hakan a raina, na fahimci yabawa ce. Sai kuma na yiwa Haidar dariyar yadda yayi da fuskarsa "wallahi idan kuka cigaba da takura min a gidan nan in na koma gidan Hamma ba zan dawo ba" ya fada yana cika bakin sa da nama kaza, Mufida ta kal lomar coconut rice ta kuma kurbi lemon pineapple gannan tace "dama yaushe zaka dawo? Ai da kansu zasu dawo da kai in ka ishe su", Mama tana cin salad din da aka zuba mata tana kallona tace "a ina kika koyi girki Safiyya?" Na dago na kalle ta sai tayi min murmushi, nace "ina so ne kawai. Ina yi a gida sosai. Kuma duk cook din da za'a kawo mana gida na kan zauna tare da ita a kitchen in koyi irin abubuwan da ta iya. Sannan in munje vacations duk abubuwan da muka ci a kasashen da muka je in naji yayi min dadi na kan nemi recife din in ringa gwadawa a gida" Abba ya nuna tuwon gabansa yace "tuwon nan yayi dadi sosai. Na menene? A ido kamar fulawa a baki kuma kamar shinkafa" Haidar yayi gyaran murya suka hada ido da Muhammad suka yi dariya, na fahimci tsokanar Abba suke yi amma ban kula su ba sai na bashi amsa cikin ladabi "shinkafa ce Abba, markada ta ake yi kamar za'a yi wainar shinkafa amma sai a tafasa ruwa da mai a ciki a ringa zuba paste din ana tukawa, Daddy yana so sanda yana iya cin abinci" Abba ya gyada kai "nima yayi min dadi sosai, Miyar ma tayi dadi " na sunkuyar da kai "na gode Abba" Mama tace "wannan salad din fa? Ban taba cin hadin salad irin sa ba" na danyi murmushi "Italian ne Mama, I Italy na fara cin irinsa shine nake mimicking, though I couldn't get all the veggies da suke using, amma da akwai wani na Morocco, yafi wannan daci sosai...." Sai kuma nayi shiru ina jin a raina kamar na saki lay ina ta surutu da yawa, ban fiye son magana akan abinda nake da shi ko abinda na iya ba sai in ga kamar show up ne. Haidar ya kalli Mufida yace "ke kuma salad din wacce kasa kika iya?" Tace "ina ruwan ka? Kai na wacce kasa ka iya?" Ya matso da kujerar sa kusa da ni "duk abinda yaya ta ta iya na iya nima, in kin isa ke ma ki hada kayan ki ki koma wajen ta" daga nan sai musun wanda yafi kusan ci da ni ya kaure a tsakanin su. Mama ta zuba soup a bowl ta dara sha, na fahimci kamar ba ta son cin abinci mai nauyi da daddare. Ta dago tana kallon yadda nake ta juya shinkafa na kasa sakin jikina in ci duk kuwa da cewa ina jin yunwar, tace "Hajjo ta bani labarin mahaifiyar ki sosal. She was an incredible woman and I believe you are too. I wish I had the privilege of meeting her amma Allah bai yi ba, but na samu privilege na meeting you. Ina so ki sauke ni a matsayin ta, duk abinda kike tunanin zata iya yi miki idan da ace tana da rai nima zanyi miki shi insha Allah, Duk abinda kike tunanin zaki ¡ya zama ki gaya mata nima zaki iya zama ki gaya min. Kar kiyi considering Gidado a cikin relationship din mu ballantana har ki dauke ni a matsayin in-law. Ina so ki dauke ni a matsayin uwa kamar yadda ni mana dauke ki a matsayin ya" Abba ya ajiye spoon din hannunsa yana karbar bowl din da Mufida da zuba masa fruit salad yace "that goes for the rest of the family" ya shafa kan Gidado da yake gefensa yana cin abincin sa duk abinda ake bai ce komai ba yace "Gidado is just a bridge da yayi leading din ki to us. But you are now a daughter to us kamar yadda Mufida take. In kin kauce hanya we will guide you. In kinyi dai da we will celebrate you and cheer you up." Nayi murmushi "thank you Abba" ina jin Muhammad yana zunguri na da kafarsa ta kasan table din amma ban nuna na san yana yi ba. Bayan mun gama su Muhammad suka fita masallaci sallar isha mu kuma muka shiga ciki muka yi. Dakin Mufida na shiga nayi sallar a can ina kallon dakin yadda yake kamar ba ta yi aure ba, komai na ta yana nan yadda duk sanda tazo gidan she is welcome, Hakan akin Muhammad ma, kafin mu tati sai da ya ja ni ya nuna min dakin sa and I saw his old pictures har na dauki guda daya na boye a jaka ta. Muka yiwa su Mama sallama Mufida ta raka mu ¿har mota sannan muka tafi da niyyar zamu fito jibi mu raka su airport. Muhammad ne ya karbi driving din. Muna daukan hanya na kama hannun sa na matse tare da zare masa ido nace "wa na kama? Shine kake tsokana ta ko?" Ya kama dariya "kinga idon ki kuwa a gaban Abba? You looked like beran da aka ajiye a gaban cat" na nuna kaina "ni ko? Ni ce beran ko? Wai kai waye ya koya maka hausa ne da har ka ke bakar magana?" ya juyo yana kallona yace "zama da madaukin kanwa. Ke kika koya min". Gidan Daddy muka wuce. A hanya na nemi shawarar Muhammad akan wani abu da yake damuna a raina, maganar Mommy. Ina son yi mata wani abu na kyautata wa da zata ji dadi. Na fahimci duk issues din da na samu da ita sun fara ne tun sanda ta fahimci nice mai kudin gidan ba Daddy ba, na kuma fahimci tsoro ne ya saka ta yin koma me tayi, tsoron rashin madafa idan babu Daddy. Sai na tambaye shi yana gain inyi mata kyautar kudi masu tsoka haka ko kuma in siya mata wata kadara wadda zata saka ta fahimci ko babu Daddy ba zan rabu da ita ba. Sal ya bani shawarar da tafi duk wannan. Kuma sosai nayi na'am da shawarar ta sa na kuma ji dadi. A gidan na tarar Mommy ta dawo kamar yadda tayi min alkawari. A wajen Daddy na same su ita da Mustapha suna magana, Na lura maganar Safina suke yi dan haka ban saka baki ba sai na gaishe su bayan na gaishe da Daddy tare da tambayar su hanya. Ga mamaki na sai naji Mustapha yana tsokana ta wai an gaya masa ina missing din su kullum sai nazo gida, Muna cikin maganar Muhammad ya shigo, ya gaishe da Daddy sannan ya gaishe da Mommy, ta amsa masa a ciki ba tare da ta kalle shi ba sannan ta dauki jakarta ta shiga cikin gida. Ya mika wa Mustapha hannu suka gaisa babu yabo babu fallasa sai shima Mustaphan ya fita. Bayan sun fita ne na gayawa Daddy shawarar da Muhammad ya bani dazu a mota "Daddy ina so zan bawa Mommy five percent share in one of my companies" ya danyi shiru yana kaliona amma na ga jin dadi a fuskar sa sannan yace "why? Menene dalilin ki nayin hakan?" Nace "kawai ina jin babu dadi ne, bata da wata kadara in her name, bata da wani source of income, duk wata bukata da zata taso mata sal dai ayi mata. She deserves better. Shine nake gain idan na bata share din zata samu source of security sannan zata ke samun wani abu yana shigo mata yadda ba zata dogara da sai anyi mata wasu kananan abubuwan ba. Na san in na bata kudi zata kashe su ne, in na bata wani abu ma zata iya siyarwa. Amma hannun jari will be there kuma zata ji a ranta cewa ita ma da ita a cikin dukiyar nan. Amma sai abinda kace" ya danyi murmushi ya kalli Muhammad duk kuwa da ban gaya masa Muhammad din ne ya bada shawarar ba, sannan ya gyada kai cikin amincewa "hakan tunani ne mai kyau. Allah yayi muku albarka. Aikin Mustapha fa?" nayi murmushin jin dadin amincewar sa sai nace "aikin Mustapha yana nan kamar yadda na gaya masa, duk sanda yake so za'a bashi list of all available positions ya zabi wanda yake so a ciki, Kuma munyi magana yace zai zo. Maganar Mommy kuma I will ask barrister Umar to take care of all the paperwork sai mu kawo maka kai kuma ka bata". Maman Maama ✍🏻 [07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹 Episode Seventy One: The Travelers Afuwan. Network ya rike min komai tun jiya. Mun dai kusa gamawa. One more episode to go. .......... Please masu tambayar document, like I said kafin in fara typing paid episodes din Safiyya, babu document. In mun gama l will arrange the episodes in the group yadda zai yiwa kowa dadin maimaici. Insha Allah. Muna fitowa muka had da Dr Ma'aruf zai shiga, sai muka tsaya muka gaisa ya sake taya mu murnar auren mu sannan ya bani update akan lafiyar Daddy, as I expected, ba update bane mai dadi, amma yayi amfani da kalamai masu kwantar da hankali kawai dai ya nuna mana we should expect anything at any moment. A mota I was feeling down sai Muhammad ya dan fara yi min hira yaji bana amsawa sai ya barni. A hanya muka tsaya a wani fast food joint ya shiga ya lodo mana kayan ciye ciye wai ya ga ban ci abinci sosai ba dazu, ya dauko min different varieties of ice cream saboda ya san ina so, daga baya ya kwaso chocolates na dairymilk duk dan ya ga na dawo da fara'a ta, i tried appreciating him duk da dai still hankali na yana kan Daddy da yadda yake jin jiki. Bayan mun sake hawa titi sai ya kunna kida kasa kasa muna tafiya muna ji, daga baya kuma sai ya fara bi with that deep voice of his, na dan juyo ina kallon sa ina jin yadda yake bin wakar kamar shine ya rubuta ta for me, lyrics din tas a bakin sa 🎶🎶I took an arrow to the heart I never kissed a mouth that tastes like yours Strawberries and somethin' more Ooh yeah, I want it all🎶🎶 🎶🎶Mm, you got me feelin' like I wanna be that guy, I wanna kiss your eyes I wanna drink that smile, I wanna feel like I'm Like my soul's on fire, I wanna stay up all day and all night Yeah, you got me singin' like🎶🎶 Ganin ina kalion sa sai yayi murmushi tare da sarkafe hannun sa cikin nawa yayi kissing ya cigaba da bin wakar, 🎶🎶Ooh, I love it when you do it like that And when you're close up, give me the shivers Oh baby, you wanna dance "til the sunlight cracks And when they say the party's over, then we'll bring it right back And we'll say, ooh,🎶🎶……. nima sai na samu kai na da bive masa na fara bi nima, 🎶🎶Into the car On the backseat in the moonlit dark Wrap me up between your legs and arms Ooh, I can't get enough You know you could tear me apart (ooh) Put me back together and take my heart I never thought that I could love this hard Ooh, I can't get enough Mm, you got me feeling like🎶🎶 🎶🎶I wanna be that guy, I wanna kiss your eyes I wanna drink that smile, I wanna feel like I'm Like my soul's on fire, I wanna stay up all day and all night Yeah, you got me singin' like🎶🎶….. tun muna yi a hankali har muka fara raising voices din mu ina using hannun sa as microphone shima yana using nawa, wakar ta kare sai wakar "shape of you" ta fara, muka cigaba da bi cikin nishadi har ta kai karshe itama sai aka fara "south of the border" 🎶🎶She got the, mmm, brown eyes, caramel thighs Long hair, no wedding ring, hey I saw you lookin' from across the way And now I really wanna know your name She got the, mmm, white dress, but when she's wearin' less Man, you know that she drives me crazy The, mmm, brown eyes, beautiful smile You know I love watching you do your thing I love her hips, curves, lips say the words Te amo, mami, ah, te amo, mami 1 kiss her, this love is like a dream🎶🎶 🎶🎶So join me in this bed that I'm in Push up on me and sweat, darling So I'm gonna put my time in I won't stop until the angels sing Jump in that water, be free Come south of the border with me🎶🎶 🎶🎶He got that, mmm, green eyes, givin' me signs That he really wants to know my name, hey I saw you lookin' from across the way And suddenly, I'm glad I came, ay! Ven para acá quiero bailar, toma mi mano Quiero sentir tu cuerpo en mi, estás temblando Mmm, green eyes, takin' your time Now we know we'll never be the same........🎶🎶 Muhammad ya fara bin ta ni kuma ban iya lyrics din ba amma naki hakura sai nayi ta zuba shirme na, ai kuwa ya kama min dariya amma na maze naki dainawa na cigaba da fadar duk abinda yazo bakina a dole wakar nake bi, dariya sosai yake yi sam ya manta ma da driving yake yi, dan ma a hankali yake tafiya. Allah ne dai kawai ya kai mu gida lafiya, a gidan ma a tsakiyar compound yay packing muka cigaba da bin wakar "wild thoughts" da ta fara a lokacin, itama ban iya ba, haka muka fito kan compound din muna bin waka muna dariya, in ka ganmu zaka dauka a buge muke saboda yadda muke dariya muna magana muna waka at the same time, kofofin motar ma duk biyun a bude muka bar su, wakar ta dauke sai na fara wakar kidz Daniel ta "marhaba", Muhammad bai iya ba amma sai ya dage ya fara bi, ni dai ina jin har da fulatanci, larabci da gwaranci ya hada a cikin wakar nan, dariyar da nayi har sai da na kai kasa na zauna dirshan ina dariya kamar ciki na zaiyi ciwo, kuma bai daina ba, na tabbatar shi kansa bai san me yake cewa ba. Sai da ya hakura dan kansa sannan ya bari, ya mika min hannu na kama ya jani na tashi tsaye still ina rike da cikina saboda dariya, sai kuma yace "let's see who will be the first to reach the top!" Muka kwasa a guje, na wuce shi a waje amma muna shiga ciki yayi overtaking dina, na rike rigar sa na jawo shi baya muka fadi a wajen, ya sake mike wa da gudu nima na bishi sai dai a kasan stairs na tsaya ina haki saboda already dariya ta cinye min duk karfina, amma shi da gudu ya haye saman stairs, sai da ya kai karshe sannan ya juyo yayi min gwalo, na daga murya "wallahi ban yarda ba, ai ban shirya ba. This is cheating" yace "cheating ya wuce rike nin da kika yi? Was that not cheating?". Na zubar da takalma na da jaka ta a wajen na kwanta a kasa "Ni wallahi ban yarda ba wayo kayi min, Allah sal ka dawo an sake" na fada ina bubbuga kafa a kasa, Sai da ya dawo kuwa, amma da ya davo ba racing din aka sake ba sunkuyawa yayi na hau bayansa ya hau dani saman dan cewa nayi na gaji ba zan iya hawa ba. A falon sama ya ajiye ni, sai a lokacin muka tuna da ledojin da muka siyo, ya koma mota ya dauko ya dawo muka baje anan falon muka ci abinda zamu iya ci sauran ya kwashe ya kai fridge, ni kuma na gyara gurin na saka turaren wuta to get rid of kamshin abinci sannan na bishi kitchen na tarar yana dafa tea sal na zuba masa spices din da nake using for tea ya sake re-boiling, sai dai kuma tunda ya juyo kaina muka manta da tea, sanda muka tuna da tea din already har ya sake hucewa dan haka muka sake boiling for the third time. Bayan tafasa ta ukun ma bamu sha ba dan sanda ya tafasa ya kashe kansa bama duniyar nan, muna can a ta ma'aurata muna shawagi. Washegari da safe a dakina muka farka. Mun jima a kwance idon mu biyu amma kowa da tunanin da yake zuciyar sa, na fahimci ya farka ne kawai saboda ji da nayi ya kara matsowa jiki na hannun sa a ciki na yana shafa fatar cikin, ni tunanin Daddy nake yi ina lissafin hanyar da zanyi easing rayuwa for him, Mun jima a haka tannan naji dan yatsansa yana tracing scar din da take cikina, na bude ido na da yake rute amma bana ganin sa tunda a baya na yake, sai naji ya danyi gyaran murya sannan a hankali yace "yana ina?" Na mayar da idanuna na rufe ina jin zuciya ta tayi nauyi, na sani cewa it takes a lot of courage and love for Muhammad to ask me about Junior. Na san dole zasu hadu watarana kuma dole zasu y interacting in one way or the other amma banyi niyyar matsawa Muhammad ya kula Junior ba, Junior da na ne, ni kadai. Na bude ido ban ce komai ba sai ya sake ja na jikinsa ya dora fuskar sa akan tawa duk muna kallon side daya ya sake cewa "where is he?" Na danyi tunani sannan a hankali nace "maybe at uncle Sufyan's. Or on the road. Or at the airport. Or on the plane. I am not sure. Na san dai yau zasu tafi Berlin". Ya danyi kissing gefen wuyana sannan yace "call them. In basu tafi ba we will go and see them up" nayi sauri na juyo ina kallon sa amma bai kalle ni ba sai ya mike ya sauka daga kan gadon ya shiga toilet. Kitchen na tafi, na jima a tsaye ina dafe da worktop ina jin effects din daren jiya a jikina, sal na samu kaina da tambayar kaina haka duk amare suke ji? Amma na san a hankali jikin nawa zai saba da auren. Na girgiza kaina da murmushi a fuska ta trying not to think of the night dan in samu in yi functioning properly. Stool na jawo na zauna akai sannan na kira Daddy a gaishe shi na duba jikinsa, na san karfin hali yake yi dan har da tsokana ta yayi, sai kuma na kira Abdul, half expecting cewa kiran ba zai shiga ba dan ina tunanin already suna cikin jirgi amma sai naji ya shiga, ya dauka "amarya" nayi murmushi "na'am ango" sai yayi dariya "ai mun girma mu, mun bar muku wannan title din" nace "na karba da hannu bibbiyu" yace "ohh da gaske? Ko alkunya babu?" Ban amsa ba sai nace "ya kake? Ya Hafsa?" Yace "Lafiya lau, gashi nan muna shirye shiryen bar muku wanna kasar ta ku mai dan karen zafi" nace "karfe nawa jirgin zai tashi?" Yace "2, that's idan bamu samu delay ba" na gyada kai ina duba agogo nace "okay. In sha Allah zamu zo airport din muyi muku bankwana" ya danyi shiru sannan yace "ohh. Okay. To shikenan. I will see you there" daga haka muka yi sallama. Banana smoothie na fara hadawa sannan na fara shirya mana breakfast ina yi ina shan abi na, Muhammad ya shigo smelling and looking fresh, ya dauke min smoothie na ya shanye sannan ya sake re-boiling tea din mu na jiya for the forth time, ni kuma na hada mana sandwich irin wanda na san yana so tun ina school sannan na soya samosas a cikin wadanda Hajiya ta yo min. Anan kitchen muka yi breakfast din, muna hirar abinda yake raina, hirar Daddy. Sai da muka gama sannan ya tambaye ni "karfe nawa zasu tafi?" Na gaya masa sai ya mike "okay, ki shirya sai muje" daga haka ya fita. Daki na koma na shirya kamar yadda ya bukata, a raina ina hasko fidkar Junior kuma ina tunanin ko zai gane ni? Ko zai yarda yazo gurina? Ko kuma zai turo baki ¡va saka kuka kamar ranar nan? Ina gama shiryawa Muhammad ya kira ni yace zai je masjid in na yi sallar in same shi a mota, hakan ya sa nima nayi alwala nayi sallah sannan na kara gyara fuska ta na saka shades dina na yafa mayafi na fita. A gaban mota na same shi rana tana kara haske min shi, sai nayi murmushi na tsaya a bakin kofa ina kallon sa, na rasa dalilin da yasa kullum nake ganin yana kara min kyau, kullum na kalle shi sai nayi tasbihi ga Ubangijin da ya halicce shi. Duk kuwa da cewa idanunsa a cikin glasses suke sai da na gane shima ni yake kallo kuma ya san kalion sa nake yi, yayi murmushi tare da yi min alamar "what?" Da hannun sa, ni kuma nayi masa alamar "kayi kyau" tare da blowing masa kiss. Sai ya tako ya karaso inda nake tsaye, na langwabe kai gefe nace "you look so handsome" and I saw his face turned red, sannan ya mika min hannun sa na kama muka taka zuwa inda motar take ya bude min na shiga ya rufe sannan ya zagaya ya shiga gurin driver. Ina kallon security suka shiga tasu motar, sannan ya tayar muka fita. Tun da muka fita yaki kallon titi completely, hankalin sa duk yana kaina, a karshe dai sai ya ja motar zuwa gefe yayi packing, na juyo zan yi mishi magana sai naga ya cire glasses din idonsa ya kamo fuska ta zuwa ta sa ya fara kissing dina, sai da yayi mai isarsa sannan ya sake ni, na bude ido da mamaki ina kallon sa sai naga ya kara fadada murmushin fuskarsa sannan yace "much better" na bata rai nace "what? A titi fa muke" ya daga kafada "I don't care" sai kuma ya ja motar muka yi gaba. Ya dan juyo ya kalle ni yace "those lips are a bomb even without a lipstick" na yi sauri na taba lips dina sannan na jawo mirror na kalli fuska ta, Ya goge min lipstick tas, Na bata rai tare da hararar sa yayi dariya, "ko gobe kika kara sakawa in zamu fita sai na goge shi" nima sai nayi dariya ina kallon tasa fuskar, ya bata rai tare da tambayar "what?" Na nuna masa mirror, ya jawo ya duba sai na kara yin dariya, lipstick din da ya goge daga nawa bakin duk ya koma nasa, nace "dama ai mugunta fitsarin fako ce" ya bata fuska yace "menene fitsarin fako?" Na yu masa bayanin karin maganar da kuma ma'anar ta, ya tura baki irin yadda nake yi yana kallon kansa a madubi sai na kara yin dariya, na jawo tissue na mika masa sai ya juyo min da fuskar na goge masa sannan na gyara tawa fuskar. Sai da muka je airport sannan na kara fahimtar dalilin goge min lipstick dina, Abdul yake kishi, ni sai a lokacin ma na tuna da na gaya masa har da shi aka yi kokarin hada ni aure, amma ai bance masa yana so na ko kuma ni ina son sa ba sai dai kiri kiri ya hana ni tsayawa muyi magana da Abdul din. Da ma muna zuwa suma suna zuwa, Abdul ne ya fara zuwa wajen motar mu da niyyar mu gaisa amma Muhammad ya zagayo side din kofa ta yayi bake bake ya hana ni magana, dole Abdul ya juya ya tafi yana shigar musu da kaya ciki. Na juya ina kalion Muhammad sai ya daga katada sannan ya bude min kofa na fito "babu dad fa haka. Abdul yana da kirki sosai. Kuma shima ai yana da matarsa" yace "ina ruwa na da matarsa, Ya tafi gurin matar ta sa mana waye yace yazo gurin tawa matar?" Murmushi kawai nayi dan na fahimci ba zai fahimta ba. Na tafi wajen Aunty Hajjo da uncle Sufyan a gaishe su cikin jin kunya. Muhammad shima ya karaso ya gaishe su. Ban ga Junior a hannun su ba kuma ban tambaye su shi ba. Muka danyi maganar jikin Daddy da Uncle Sufyan sai shima ya shige ciki, a lokacin ne Hafsa ta karaso inda muke hannun ta rike da Junior. Ta tsaya muka gaisa tana tsokana ta wai ina kyallin goshi irin na amare, ta koma kan Muhammad shima wai tun da muka zo gurin ni yake kallo kamar ba tare muka taho ba. Junior ne ya ja sarkar wuyanta da karfi, ta dan yi kara ni kuma nayi saurin rike hannunsa "Hey! Baka ji ko?" Na fara kokarin cire sarkar daga hannun amma ya dintse hannun, tace "karfi ne fa da wannan yaron da kike ganin sa" na kasa cire sarkar daga hannun sai na balle mata sarkar daga wuyanta, ai kuwa yana ganin mun cire sarkar sai ya saka daya hannun ya kama dan kunnen ta guda daya har yana dariya. Na kama hannun a dan daka kadan tare da zare masa ido "let it go!" Na fada ina kalion sa cikin ido, sai ya kyalkyale da dariya yana bayyana hakoran sa guda biyu. Hafsa ta zaro ido "kar ki yarda Mama ta ganki kina dukan bundle of joy din ta" Aunty Hajjo da take gefen mu tayi gyaran murya tace "ina kallon ta aj" na danyi murmushi ban ce komai ba, dan kunnen na cire daga kunnen Hafsa, Junior ya koma hannu daya sarka hannu daya dan kunne. Ya juyo yana kallona sai na harare shi sai ji nayi yace "ehh!" Kamar me cewa "hey" irin yadda nake ce masa, sai kuma va saki sarka da dan kunnen suka zube a kasa ya miko min hannu. Hafsa cikin mamaki tace "what? Yaron nan fa baya zuwa gurin kowa" Na dan fara ja da baya "kwadayayye ne. Ya tuna ina bashi sweet" sai ta miko min shi "hold him. Bara in duba kaya" na karbe shi "ehh!" Ya kara fada yana nuna min hannunsa "bani da sweet" na fada ina kallon sa "ban zo da sweet ba". Muhammad ya karaso kusa da mu. Sai a lokacin na fahimci mu kadai ne a wajen Aunty Hajjo ma ta zagaya wajen kayan su da ake shiga dasu ciki. Na daga kai ina kalion sa sai naga yana kallon Junior, expression din fuskarsa unreadable. Ya ciwon hannayen sa da suke aljihu ya mika masa "come" nan take Junior ya bata rai ya turo baki idonsa ya cicciko da kwalla. Muhammad ya bude ido "me nayi maka? Shari zaka yi min?" Ai kam nan take ya balle da kuka, sai naga Muhammad yana dariya sannan ya lakuce masa hanci '"shagwaba irin ta gado". Na harare shi amma bance komai ba. Sai ya karbe shi daga hannuna ta karfi yace "tunda kayi min sharri sai na dauke ka" ya cigaba da kukan sa Muhammad yana jijiga shi sai kuma ya bar gurin da shi, har Hafsa ta dawo basu dawo ba, sai muka shiga ciki tare da ita muka tarar an gama auna musu kayansu ana clearing din su, Abdul ne ya tambayi inda Junior yake babu wanda ya bashi amsa sai yayi shiru, sai can daga baya kuma sai ga su nan sun taho, na bisu da kallo har suka karaso, hannayen Junior biyu rike da sweet ga kuma leda a hannun Muhammad. Da yazo kuma sai ya rasa wanda zai mika wa shi, sai ya mika wa Abdul. Da murnar sa yaje gurin Abdul din amma sai ya juyo yana kallona yace "ehh!" Sai ya mika min sweet din hannunsa, naji kunya ta kamani amma ganin kowa yana kallo na sai na saka hannu na karba tare da cewa "thank you" ya gyada kai kamar ya gane abinda nace sannan ya bude tasa sweet din ya saka a baki, Aka kira sunan jirgin su sai muka yi musu salama suka shige. Abdul ne na karshen shiga, ya dago hannun Junior da yake rungume da ledar kayan dadin sa yayi mana bye bye. Muhammad ne ya daga musu hannu ni kuma sai a bisu da murmushi kawai. Na bisu da kallo kawai wandering what life might have in store for Junior and for us. Kamar yadida Mustapha yay min alkawari, ranar suka zo tare da twins bayan mun koma gida. Suka taho min da motoci na na gidan Daddy. Lokacin Muhammad ya fita yaje gida, sai na saka hijab na sauka kasa gurin su. Anan suka ci abincin rana, I gave him list of job vacancies din da muke dasu kuma ya zaba a take kuma na rubuta masa offer na tura masa zuwa e- mail din sa tare da tura wa uncle Ahmad a matsayin sa na chief of staff dina dan ya sani kuma yayi referring Mustapha zuwa department dinsa. Sai kuma a ce da Mustapha "be nice to uncle Ahmad. Na san halinka. Kar kayi masa rashin kunya ku zo kuna rigima dan Allah, Babana ne shi and you have no idea what he is going through" murmushi kawai yayi ya kalli twins da suke gurin yace "ba zan yi masa ba. Na girma ai yanzu" dariya muka yi gabakidaya, Sai ya bani labarin maganar auren da Daddy yace masa yayi, naji dadi nace "ina yammatan da ka ce min suna ta bin ka?" Ya bata rai "wasa nake miki fa. Ni bani da wata budurwa. Ki nemo min" murmushi kawai nayi na bar maganar. Daga nan muka yi maganar tafiyar twins karatu, komai ya kammala zuwa karshen watan nan zasu tafi insha Allah. Duk da dai na fahimci kamar basa son tafiya su bar Daddy amma kuma Daddyn ne mai matsawa akan tafiyar ta su yace baya son ciwon sa ya tsayar da rayuwar mu a guri daya. Ban tambaye su labarin Safina ba suma kuma basu yi min ba. Sai da suka zo tafiya sannan Hassan yake ce min "gobe za'a je a kwashe kayan yaya Safina a kai mata Katsina, tare da sabuwar motar da Yaya Muhammad ya siya mata, har kayan ta da suke gidan mu ma tace duk a kwashe su a kai mata Katsina" Hussein yace "Mommy bata ji dadin hakan ba, Daddy ma haka. Amma sun ce a barta for now ta huce da kanta ta gane gaskiya" Hassan yayi ajiyar zuciya yace "maybe it is for the best" ban ce komai ba, su ma kuma babu wanda ya sake cewa komai, Sal da suka zo tafiya na rako su waje sannan Mustapha yace min "about that son of hellfire. Ban manta da shi ba fa. Abubuwa ne suka yi min yawa kwana biyu shi yasa na ajiye shi a gefe, amma zan waiwaye shi very soon" na fahimci zancen Mukhtar yake yi sai nayi murmushi nace "bana jin akwai abinda yayi saura a tattare da shi da zaka dauka, And if I am to advise you zan baka shawara akan ribar barin komai a hannun Allah, Sakayya sa tafi duk abinda kake tunani girma" sai yayi murmushi tare da gyada kai yace "I will think about that". Sai da suka shiga mota sannan yace min "congratulations fa, Allah ya sanya alkhairi" nayi murmushi "Amen ya Rabbi. Allah ya nuna mana na yan baya". Washegari da wuri muka shirya muka tafi gidan Abba, muka tarar already har sun shirya abu kadan ya rage musu, naji dadin yadda Mama tayi involving dina a gyaran gida tace in shirya mata bedroom dinta in rufe komai in adana komai yadda zai zauna as it is har su dawo, I did the best that I can. Daga nan muka hadu gabaki daya a ….…….din gidan. Ni da Mufida ne a can baya, Abba da Mama a tsakiya sai Muhammad a gaba Haidar kuma yana driving, Wasa da dariya kawai ake yi a cikin motar, Haidar ya dage wal su Mama honeymoon zasu je, Abba yace ina ruwan sa matar sa ce ko ta sa? Ni dal bana magana sal an saka ni a ciki kuma na lura sosai suna kokarin saka ni a cikin magana in suna yi, Muhammad ne ma bai fiya yi min magana directly ba, na kuma lura suna kokarin yin turanci da few hausa words duk dan saboda ni amma idan su kadai ne sun fi yin fulatanci, Bayan munje airport Mama da Abba took their time to hug each and every one of their kids, Mama ta zo kaina and she hugged me too, sai na samu kaina nima da rungumar ta ina murmushi. Na dago kaina muka hada ido da Muhammad naga yana murmushi fuskarsa dauke da farin ciki, it was like a dream come true for him. Abba bai rungume ni ba duk da da cewa yanzun shi muharrami na ne, sai dai he smiled at me and told me to take care of myself, ya kuma kara da cewa "idan Gidado ya dame ki ki kira ni ki gaya min". Murmushi kawai nayi na sunkuyar da kai. Sai da suka shiga ciki sannan muka koma, kiri kiri Muhammad ya kwacewa Mufida guri ya dawo baya wajena dan ya dame ni, ita kuma ta koma gaba, Muna barin airport din Haidar yace "Fiyya, wallahi kar ki yarda, ki ga Abba ya tafi da Mama honeymoon amma ke naki angon airport kawai ya kawo ki? Gaskiya da sake" Muhammad ya daga murya yace "idan na tafi da ita kai zaka rasa kwanon abinci. Ai dama mugunta fitsarin fako ce" Haidar ya juyo ya kalle mu yace "menene fitsayin fako?" Dariya muka yi ni da Muhammad sannan na lakuce masa hanci nace "you are a very good student Malam Muhammadu" shima ya rama ace "you are a very good teacher Safiyya Adam" daga nan muka kama hirar irin maganganun hausa da na koya masa, muka tuna sanda na fara koya masa cewa mutum karyarsa bata sallah, ranar yayi dariya kamar me ..…. Gidan Mufida muka fara zuwa dan mu ajiye ta, amma sai ta jamu muka shiga ciki wai dama ban taba zuwa gidan ta ba, sai da muka zagaya ko'ina a gidan, yayi kyau sosai kuma an zuba naira ba kyar kadan ba a gidan. A lokacin ne kuma ta bani shawarar tunda ina koyawa Muhammad hausa to shima ya kamata ya fara koya min fulatanci, na kuma amince sannan na Kara jaddada masa sunan Malam Muhammad dan fillo, Ranar kam na dauki darasi sosai na fulatanci, ya koya min kalmomi da yawa, na kuma rike su, amma sanda ya gaya min ma'anar kalmomin da ya koya min sai da na toshe kunnuwana dan sunyi min girma a saurare ma ballantana a fade "Allah ya shirye ka" a fada ina kallon sa yana yi min dariyar mugunta. Allah ya so ni banje ina fada a cikin mutane ba. Ya sake jawo ni, "mun gama lesson one, come, let's start lesson two" a fara kokarin zamewa ina dariya "babu wani lesson.….na hakura da koyon fulatancin tunda ba kalmomin kirki kake koya min ba" amma sai da ya jawo ni na karbi darasin dalla dalla na kuma yi bita sannan nayi hadda. Washegari Monday Muhammad ya koma aikin sa, dama hutun sati daya Abba ya bashi, kuma kasancewar abban yayi tafiya ya saka bai karawa kansa hutun ba duk kuwa da yadda yaso yin hakan. Nima kuma a ranar ne na koma nawa aikin wanda office dina yake a cikin closet dina. Sai dai hakan ba wai raba yayi ba sai ma kara mana dokin gain juna kullum da yamma, da ranar ma kuma muna makale da juna almost all through, In ya dawo da daddare kuma kullum zamu je mu duba Daddy mu ga idan akwai wani abu da yake bukata sannan mu dawo gida. Kamar yadda Muhammad yay alkawari, da weekend muka tafi Kura local government, zamfara state. A mota muka yi deciding yin tafiyar saboda muna son ganin hanya and have the experience of being on a road trip together. Ba muyi niyyar kwana ba amma sai na hada mana kayan mu set bibbiyu just in case. A ranar ne kuma na fara using sabuwar mota ta wadda sai a ranar Muhammad ya bare ta daga cikin ledar ta. We both dress light sannan Esther ta cika mana basket da abinci da sauran kayan ciye ciye, ta kuma zubawa security suma dan Daddy ya dage tare zamu tafi da su. Muna yin sallar asuba muka dauki hanya. Wannan tafiyar was one of the best memories of our lives dan mun samu nishadi, nasara da experience sosai a cikin ta. Tun kafin mu tafi dama Muhammad ya kira wanda Abba ya hada mu da shi ya gaya masa zamu taho, sai kuma ya gaya min cewa yana da surprise for me a can. Hakan da naji sai ya saka ni cikin anticipation and kept me moody a farkon tafiyar ta mu, amma Muhammad knows his ways around me dan haka bamu jima on the road ba na manta da komai sai shi sai kuma abinda nake ji a zuciya ta game da shi din. Munyi hira, munyi dariya, munyi fada mun kuma mori soyayya, we had to park at one time a cikin inuwar wata katuwar bishiya muka danyi uzuri sannan muka muka cigaba da tafiya muna dariya akan audacity din mu to do that on the road. "Baby da wani yazo yayi knocking fa ya dauka motar ce ta lalace or something?" "Ai kuwa da sai na cire masa idanu. And the security won't let anyone come near us" "idan kuma barayi ne fa?" "Tun muna ciki ake yi mana addu'a Babe, none of that will happen insha Allah", Da muka sake gajiya kuma sai muka sake tsayawa a wani guri mai kyau da muka gani muka shimfida carpet din da Esther ta sako mana a mota muka zauna muka huta muka ci abinci muka yi sallar. A wannan lokacin ne muka yi mani major discovery a rayuwar mu, muka kuma yanke wani major decision. Mun fahimci cewa we both have a huge fashion for travelling, sannan muka yanke shawarar cewa no matter how long it will take us, zamu kai ziyara each and every one of the 195 countries of this world. A take na fara rubuta sunayen countries din da a taba zuwa ni kadai da kuma wadanda ya taba zuwa shi kadai sannan da wadanda muke so mu fara zuwa a tare. A lokacin ne ya gaya min wani abu da ban sani ba, "I planned our honeymoon tun sanda na fara tunanin za'a daura mana aure. I booked and paid everything bayan an daura auren an kuma saka ranar biki. Idan zaki tuna first night din mu together akwai wasu takardu da na fito da su tare da rings din nan" na tuna ganin takardun amma abinda ya faru ranar ya mantar da ni bibiyar su, na bude ido cikin mamaki "then why are we still here?" Ya dan sosa kan sa sannan yace "I saw jikin Daddy, and I know you won't want to be away from him in that condition. Sai na fasa. I cancelled everything. Yanzu ba gashi muna honeymoon din mu ba anan?" Ya fada yana nuna gurin da muke, nayi dariya amma kuma maganar sa ta taba min zuciya ta sosai kuma ta kara masa kima da daraja a cikin zuciya ta. Ina matukar jin dadin yadda yake da damuwa akan duk abinda ya dame ni. Wadannan delays din da kuma kasancewar ba gudu muke yi ba ya saka ba mu je Kura ba sai la'asar. Sai da muka je garin sannan jiki na yayi sanyi, Muhammad ya kira Alhaji Abubakar ya gaya masa mun shigo gari shi kuma yayi guiding din mu zuwa gidan sa. Gida ne mai kyau, shima kuma babban mutum ne mai karamci, iyalansa ma haka. Anan muka samu tarba mai kyau, ga abinci ga nama da fura da nono. Bama jin yunwa amma sai da na dan ci kadan duk kuwa da girgiza min mai da Muhammad yake yi wai ba'a cin abinci a bakon guri, ni kuma na ci ne dan suji dadi. Albishir din da suka yi min shine tun kafin mu z0 Muhammad ya bawa Alhaji information din da ya samu daga Daddy, shi kuma already yayi bincike kuma ya gane wanne Alhaji Haladu ake magana akan sa. "Ban san mahaifiyar ki ba amma na san yayan sa da yawa, na san shi marigayi Malam Jamilu (yaya Malam), na san kanin sa Dauda wanda yayi ajalinsa. Na kuma san marigayi Alhaji Balarabe, na san da yawa daga cikin yayansa maza. Da yawa daga cikin su sun rasu, amma a yanzu dai akwai mutum uku da na sani wadanda suke raye a mazan ban sani ba ko bayan su akwai wani. A matan kuma wadda na sani ita ce Fatsima" na dago kai ina kallon sa dan ban san Fatsiman da yake magana a kanta ba, ban taba jin an ambace ta a yan'uwan Ammie ba. [07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: "Ban san mahaifiyar ki ba amma na san yayan sa da yawa, na san shi marigayi Malam Jamilu (yaya Malam), na san kanin sa Dauda wanda yayi ajalinsa. Na kuma san marigayi Alhaji Balarabe, na san da yawa daga cikin yayansa maza. Da yawa daga cikin su sun rasu, amma a yanzu dai akwai mutum uku da na sani wadanda suke raye a mazan ban sani ba ko bayan su akwai wani. A matan kuma wadda na sani ita ce Fatsima" na dago kai ina kallon sa dan ban san Fatsiman da yake magana a kanta ba, ban taba jin an ambace ta a yan'uwan Ammie ba. Sai yace min "Fatima kawar yayar mai daki na ce, Ita ce karama a cikin yayan Alhaji Haladu kafin a haifi yayan amaryar sa da suka rasu. Sanda na gane gidan da Kuke nema sal na saka ita mai daki na ta je har gida ta gaya mata labarin ki da kuma labarin zuwan ki. Matar nan har kuka tayi na murnar zata gan ki. Na tabbatar kuma ke ma zaki ji dadin ganin ta idan kuka je". Mai dakin na sa ita ta yafa mayafin ta duk kuwa da girman ta suka rakamu ita da yar autar yar ta. A fadar ta cewa tayi inda zamu je babu nisa ba sai mun shiga mota ba, dan haka muka bar motocin mu a kofar gidan muka bisu a baya Muhammad yana rike da hannu na yara da sauran yan gari suna kallon mu kamar wasu aliens musamman saboda security din da suka yi bake bake a bayan mu. Dan wulakancin Muhammad wai har da cewa idanun mutanen garin mu zai saka mishi allergic reaction. Ai kuwa na ce sai na rama duk sanda muka je yalleman. Sai da na fahimci kokarin kwantar min da hankali yake yi yana bani assurance cewa yana tare da ni, ni kuma tunani na yana kan wannan Fatsiman da aka ce yayar Ammie ce, ban taba ganin wani dan uwan Ammie ba tunda nake a duniya. Gurin da dan nisa, dan ni kam har sal da na gaji da taliya amma ban gaji da ganin gari ba, Na bude ido sosal ina ta kallon titinan su da layukan su in imagining Baba Hadiza yadda take yawon tallan abinci, nayi imagining Ammie da sisters din ta suna tafiya makaranta, musamman da muka zo muka wuce ta gaban wata primary sai matar ta gaya mana wanna makarantar Ammie na tayi. Jin hakan ya saka na bude ido sosai ina kallon ta nace "kin san ta?" Sai tayi murmushi tace "seat din mu daya a primary one". Daga nan sai ta fara bamu labarin abinda zata iya tunawa na Ammie, "tana da wayo sosai kamar ba yar fari ba. Tana da dogon gashi. Ina tuna wa da yadda take tsananin son kanwarta Sauda wadda suke zuwa makaranta tare, da yadda saudan take makale mata" sai naji hawaye yana taruwa a ido na. A hanya na kira Daddy na gaya masa abinda muke ciki, dama tunda muka taho muke waya da shi. Sai ace ya kira Alhaji Jamil dan Hajiya Kyauta marigayiya wanda har yanzu sun communicating da Daddy musamman akan maintenance na masallaci da boreholes din da aka yi wa Baba Hadiza a garin, Ya turo mana number din sa yace mu kira shi idan muna bukatar wan abu. Bayan mun wuce primary din ne muka je gidan, Gidan kasa ne wanda dakunan ne kawal na kasa amma an zagaye shine da kara, muna zuwa zamu shiga sal nace da Muhammad ya tsaya a waje amma sai ya rike hannuna ya tsare ni da ido kamar wanda aka cewa in na shiga ba zan fito ba, a dole muka shiga tare. Guards din ne suka tsaya a waje da kyar. Matar tana zaune akan yar baranda a kofar dakin ta tana tankaden garin tuwo, gefe kuma ga murhu nan an hada wuta an dora tukunya, muka shiga da sallama. Ta amsa mana sannan ta bi yar rakiyar tamu da kallo "Hajiya Hajara?" Sai kuma ta kalle mu, idonta ya tsaya a kaina, ina kallon sanda idanuwan suka bude cikin mamaki sannan ta mike da sauri kamar zata fadi. Na saki hannun Muhammad na karasa gare ta ina kokarin durkusawa in gaishe ta sai ta jawo ni jikinta hawaye suna bin idonta "safiya! Jama'a ga Safiya! Ashe ina da rabon ganin ki kafin in bar duniya Safiya?" Ta sake ni tana sake kallo na, nima fuskar tata nake bi da kallo, ba zan ce suna kama da Ammie ba amma suna yanayi, ina ganin Ammie a fuskar ta, ta sake mayar da ni jikin ta ta rungume ni ma sai na samu kaina da rungume ta ina jin hawayen da nake rikewa tun dazu suna gangaro min, Ta sake ni ta fara zagaye gidan "mai gida! Mai gida! Harisu! Saminu! Ke Hannatu! Ku fito ga yata nan tazo! Ku fito ga diyar Safiya ta zo". A take mutane suka fara shigowa gidan nata, wannan ya sa guards dina suka shigo suma idanunsu a kaina suna observing duk wanda zai taba ni, ina kallon Muhammad a tsaye a gefe hannun sa a cikin aljihunsa yana kallona. Wadanda ta kira suka firfito daga dakunan su suna ta kallo na kawai. Sai da ta nutsu sannan ta gaya min samarin yayanta ne, magidancin kuma mijinta ne, yar budurwar da ta kira da Hannatu kuma ita ce autarta sauran duk ta aurar da su. Sai da ta gama murnar ta, muka gama kukan mu ni da ita, sannan ta dauki tabarma ta shimfida wa Muhammad ya zauna muma duk muka zauna. A lokacin take bamu labari "sanda Baba ya auri Baba Hadiza nice auta a gidan, dan haka daga ni sai safiya. A shekaru da kadan Baba Hadiza ta girme min dan ina da shekaru sha biyu ita kuma tana da sha hudu sanda Baba ya aure ta. Wannan yasa a gidan nice zan ce mun saba da ita dan nice kusan sa'ar ta, tare muka ringa shiriritar kuruciyar mu, kuma ina nan gidan ta haifi dukkan yayanta guda uku, sai bayan haifuwar Khadijah ne aka yi min aure kafin rasuwar Baba. Dan haka ni nati kowa sabawa da Safiya. Amma kuma ni karama ce a cikin yan'uwa na muryata bata da karfin da zan saka ko kuma in hana yin wani abu a gidan mu. Duk abinda akayi musu bana jin dadi sai dai bani da bakin magana, iyakaci in mun ware da yan'uwa na inyi mita shima da zarar sun yi kaina da fada dole in yi shiru. Mutuwar sauda da batan Safiya suna daga cikin tashin hankalin da ba zan taba mantawa da shi a rayuwata ba. Tun daga nan kuma na fara kukan yin shiru da nake yi. Na fara neman yadda zanyi in samu Safiya. Amma ni bani da hali. Mijina bashi da karfi. Lokacin da labari yazo min cewa safiya tazo garin nan har taje gidan mu ranar ko takalmi babu haka naje har gida amma na tarar ta tafi. Aka ce tayi kudi. A kace dan yankan kai ta aura. A ka zo aka ce ita ce mai yankan kan ma. Babu irin sharrin da ba'a yi mata ba amma babu yadda zanyi akai. Sanda aka nemo inda take naso a tafi da ni amma aka ki aka ce zan bata shiri ne. Daga nan ba na ma sanin sanda suke zuwa. Sai labarin mutuwar safiya naji. Nayi kuka sosai, wannan ya sa aka tafi da ni a lokacin amma abinda yan uwa na suka yi a gidan gaisuwar ya sa nayi nadamar zuwa. Na ganki a lokacin kina karama, kina ta kuka, amma wadanda suke rike da ke ba zasu bani ke in rike ba dan basu yarda da mu ba kuma ban ga laifin su ba. Tun daga nan duk zuwan da suke yi ban sake komawa ba dan ina gudun abin kunyar da suke zuwa yi a can. A karshe dai suka samo kudin da yayi ajalin biyu daga cikin mu, da babban yayan mu da kuma autan gidan a maza, Dauda, wanda shi nake bi. Tun daga nan sauran yan'uwa suka ce dukiyar dama ta mutuwa ce, babu wanda ya kara bi ta kan neman ki ni kuma ban san komai a kan ki ba ba kuma zan iya mayar da kaina zuwa gidan ku ba. Na sani a raina kina raye, na kuma saka raina cewa watarana zaki zo har nan gidan ki same ni. Gashi kuma yau Allah ya cika min burina" Sai da ta gama jawabin sannan tace "ya sunan kip?" "Safiyya" na amsa murya ta can kasa "suna na Safiyya". And that was how I found an Aunt. Muna gurin ta akayi sallar magrib, ta tuka mana tuwo ta zubo mana, ina kallon Muhammad ya dauki cokali yayi loma daya daga ita kuma bai kara ba. Sai daga baya na samu yin magana da Muhammad *kwana ya kama mu, Allah ya sa na taho mana da kaya" ya gyada kai yana kallon surrounding din "anan zaki kwana?" Na daga kai "yes" yayl ajjiyar zuciya, nace *kai kuma better ka koma gidan Alhaji Abubakar, na ga masaukin da yayi mana is decent, zaka iya kwana a can" ya sake kallon gidan fatsima yace "zaki iya kwana anan?" Nayi murmushi "zata ji dadi" ya dan kalli cikin gidan, "just be careful. Your security will be here with you. Kina da charge a wayarki?" Nace "eh" na rike hannunsa "I will miss you, Baby" ina jin kewarsa a raina tun kafin ya bar kusa da ni, yayi murmushi "ba yanzu zan bar ki ba ai. Let's go explore the town muga yadda yake da daddare". And it was a good idea, da farko we tried to mingle with the town people amma securityn mu suka hana mu sakewa, daga baya sai muka yi musu wayo muka dawo ta gidan fatsima muka tambayi Hannatu ko akwai inda zamu iya fita banda inda muka shigo? ta nuna mana wata kofa ta baya da aka rufe da kara muka bi muka gudu muka barsu suna gadin bakin kofa. Yawo muka yi sosai hand in hand, muka zauna a dandali muka sayi awara muka ci, ko ince naci, dan Muhammad daga guda daya sai yaki karawa nima da na cinye guda biyar sai ya hanani karawa ya bayar da sauran sannan muka sayi rake da gyada, Muhammad ya zuba mana gyadar a aljihunsa, muna tafiya a titi muna shan raken mu muna hira har muka shanve sannan muka fara in gyadar. Munyi yawo har sai da kafafuwan mu suka gaji, babu haske sosai dan haka babu wanda yake gane mu baki ne. A lokacin ne muka zo masallacin Baba Hadiza, ina ganin sa na gane shi dan ina ganin hotunan shi a wajen Daddy. Sai naga yafi min girma a ido akan a hotunan. Na tsaya ina kallon sa, Muhammad ma sai ya gane shine dan haka ya tsaya. "it is big and beautiful" ya fada, nima na gyada kai cikin amincewa "yes it is", sai na cigaba da kallon masallacin ina mamakin wai da gaske nan shine asalin gidan kakanni na, anan aka haifi Ammie, Muhammad kalle ni '"muyi sallah anan. Dama bamuyi isha ba". Muka je muka yi alwala a pumps din da suke a jere a gefe, na lura ana kula da masallacin sosai dan komai a gyare yake, na shiga bangaren mata shi kuma ya shiga na maza mukayi sallah. Na samu kaina da yin dogayen adduoin ga kakanni na da iyalin su har da su inna gaje da inna saade. Sai da na gama sannan na fito na tarar Muhammad yana jirana a waje, na lura mai gadin masallacin jajirtacce ne dan babu wanda yake bari ya shigo in dai har ba ibada zaka yi ba dan Muhammad ma da zai jira ni hana shi tsayawa yayi a harabar sai da ya fita waje sannan ya jira, naji kuma voices din yara suna ta karatun Alkur'ani, sai naji dadi sosai, a raina nayi niyyar inganta makarantar tare da yiwa mai gain abun alkhairi. Ina fitowa Muhammad ya kama hannuna muka cigaba da tafiya, sai kuma muka fahimci mun bata dan bamu san hanyar da zamu bi mu koma gidan fatsima ko gidan Alhaji Abubakar ba, a lokacin ne kuma muka lura da security mu suna bin mu a baya amma sun dan bada distance a tsakanin mu, Muhammad ne ya gansu ya nuna min su, na juya na kalle su sai chief securityn ya daga min hannu, dariya muka yi, bamu san ya akayi suka nemo mu ba kuma bamu san tun yaushe suke bin mu ba. Wani mutum muka samu muka tambaya, da kyar ya gane Alhaji Abubakar din da muke magana akai tunda mu bamu san wata inkiya ta shi ba ko kuma sunan wani dan sa, sai yace "ko kune bakin da kuka 2o gidan da zu?" Sai muka yi mamaki amma Muhammad ya amsa masa da eh sal yayi mana kwatance. Gidan muka koma muka dauki motar mu sannan Muhammad ya mayar da ni gidan fatsima da already hankalin ta ya fara tashi tana neman mu. A mota muka yi sallama, kamar ba zai barni in shiga ba. Yace "take care" yafi a kirga. Ina shiga cikin gidan kuwa waya ta tayi kara naga sunansa sai na saka bluetooth a kunne na dan na san wayar ba me karewa ba ce ba. Ranar mun kusa kwana hira da fatsima da iyalinta, ni sai naji ina jin nauyin ce mata fatsima duk kuwa da cewa yayanta ma haka suke ce mata, sai na fara ce mata Aunty, suka yi ta min dariya amma naki dainawa har dai ta fara amsawa. Tayi min hirarrakin Ammie sosai. Ta kuma bani labarikan family din mu da abubuwan da suka faru, tace su uku suka rage a mata, maza ma su uku ne. Sai jikoki wadanda suma duk sun girma sun manyanta tunda dama wadansu jikokin sun girmi Ammie ma ballantana ni. Itama da take karama yayanta gabaki daya Hannatu kadai na girma, Nima na basu Labarin abubuwan da nake ganin ya kamata su sani kamar matsayin Muhammad a gurina, amma ban bude cikina nayi magana sosai ba kamar yadda Daddy ya gargade ni, duk da dai banga alamar cutarwa a tare da su ba but time will tell. Ta saka aka dauki katifar ta ta kan gado aka yi min shimfida anan tsakar gida saboda basu da wuta a gidan, ala daura min net, na shiga na kwanta ina jin dadin iskar da take kada ni. Amma kuma dai baccin banyi wani mai nisa ba saboda kukan kwari da kuma yanayin chanjin bakon guri ga kuma sararin samaniya tarwai a kaina, Duk da haka da safe na tashi fresh saboda fresh air din da na sha. A niyyar mu da wuri zamu wuce kwatarkwashi amma taki yarda, sai da tayi ta yawo dani gidajen yan'uwa, duk sauran yan'uwan su sai da ta kaini wajen su, naga murna a idon wadansu, na ga mamaki a na wasu, sannan naga mixed feelings a gurin wadansu, sai dai ban damu ba, bana nufin kowa da sharri kuma ina addu'ar kariya daga sharrin kowa. Muhammad ya bude bakin aljihu da kudin da ban san ma ya taho da su ba ya ringa raba musu. Ai kam da yawa ya saye su da wanna kudin. Da kyar muka samu muka kwace bayan azahar muka bar garin bayan ta saka nayi mata alkawari tare da rantsuwa cewa zan dawo. Ni dariya ma na ringa yi. Tace ta zata sati daya zanyi. Na tabbatar mata zuwa nayi kawai gain guri amma tunda na gansu har sai sun gaji da ni. Daga nan Alhaji Abubakar ya hada mu da wani yaron sa muka tafi kwatarkwashi..... Bani da hope din ganin kowa nawa a can duk kuwa da cewa Alhaji Abubakar ya gaya min yana da another surprise for me, amma abinda na tarar yafi wanda na gani a Kura faranta min rai, Yayun Baba Hadiza guda biyu Jabiru da Audu suna garin a lokacin, Shi Jabiru shekaru ne suka yi masa yawa and he chose to spend the last of his days a inda iyayensa suka rasu. Shi kuma Audu wanda shine Baba Hadiza take bi ashe tun zagayowar sa garin ta farko wadda yayi musamman dan kanwar ta sa sai kuma yazo ya tarar da munanan labarai a jere, babu Hadiza kanwarsa babu yayanta. An dai ce babbar haukacewa tayi ta bi duniya saboda tashin hankalin abinda ya faru. Wannan shine last labarin Ammie da yaji. Ya kuma yi kuka tare da takaici mai yawa akan hakan dan yana son kanwarsa Hadiza sosai kasancewar ita kadai ce yar war sa mace, Daga nan bai kara barin gari ba, Dagaci ya bashi guri a bayan gari ya kafa ruga suka zauna shi da iyalinsa yana fatan watarana Safiya zata dawo kuma zata z0 ta neme su. Lokaci zuwa lokaci ya kan je Kura ko zal samu labari, amma babu labar in komai kuma shi bal ma san gurin wanda zai nemi labarin ba. Bai san kowa ba sai Alhaji Haladu sai kuma wani kanin sa. Shima kuma kanin ba'a jima ba ya rasu. Daga baya ma sai ya tarar babu gidan Alhaji Haladu an rushe anyi masallaci. Ya kan shiga masallacin duk sa da yaje yayi sallah ya fito amma bai san komai gane da masallacin ba. Shima ya manyanta, amma da kwarinsa kuma da yake jikin fulani ne babu kiba sai ya kasance girman bai kama shi sosai ba. Nayi kukan ganin su, kamar yadda suka yi nawa. Jabiru har sai da na tausaya masa na koma ni nake bashi hakuri, duk ya dauki laifin abinda ya samu Baba Hadiza ya dora akan sa, gani yake laifin sa ne tunda yazo gari lokacin mutuwar Alhaji Haladu. Amma ya tafi ya barta da kananan yara bayan ya san bata da mataimaki sai Allah, Sai da aka gana koke koke kuma aka fara murna. Fulatanci suke yi suma sai hausa jefi jefi, a lokacin na fahimci fulatanci dialect daban daban ne dan nasu ya banbanta sosai da na Muhammad. Suna gane juna amma ba sosai ba, Sai an dan hada da hausa wani lokacin kuma sai an kara bayani, shi kuma sai yayi min bayanin abinda ban fahimta ba. A haka akayi communication din. Sai inno matar Audu ta saka ni a gaba da tsokana wai maimakon ni zan ke fassarawa mijina tunda gidan mu aka zo amma shi yake fassara min. Sai kuma ta tafi wani abu da ya saka shi murmushi tare da yi min gwalo. Na harare shi sannan na tambaye shi abinda tace sai yace cewa tayi ya fi ni kyau. Ai kuwa na dage nace kishi take yi tunda ni jika ce a wajen ta tana son ta kwace min miji. Sai a fahimci Muhammad yafi sakewa da su akan a Kura. Nan da nan aka yanka kaji aka soya mana su aka dama mana kunun nono, kunun yayi min dadi sosai har sai da na tambayi Khadija autar Baba Audu ta koya min yadda ake yi. Muka ci sosai muka koshi. Muhammad da kansa ya ce wa dan rakiyar mu ya koma anan zamu kwana, naji dadin hakan sosai, suma kuma mun raba dare da su muna hira. Sai naji nafi sakin jiki da su, na basu labaran duk abinda ya faru da kuma rasuwar Ammie na tare da matsayina a yanzu. Sunyi mamaki sosai sun kuma yi jimami tare da godiya ga Allah. Sai na basu labarin Daddy na da halin da yake ciki na rashin lafiya. Baba Audu yayi shiru sannan ya tambaye ni abinda yake damunsa, na yi masa bayanin cutar duk da bansan sunan ta da hausa ba ballantana da fulatanci. Sai yace "dan zaku tafi zan bi ku in ganshi. Zamu warkar da shi da ayar Allah tare da sauyoyin mu na daji" Maman Maama✍🏻