[8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS Page 1 GIDAN ALI Lokaci zuwa lokaci take kallon agogo tana ƙwafa, kana kallon fuskarta za ka gane cike take da ɓacin rai, ƙarfe tara tana cika cif ta ɗauki hijjabi ta saka ta ɗakko mukullin gidan ta fita ta kulle, ta ja tinga ta tsaya a ƙofar gidan, ba ta yi minti goma ba ta jiyo ƙarar babur, tana juyawa ta ga shi ne ya shawo kwana kamar yadda ta yi zato, ta ƙara haɗe gira hannunta harɗe a ƙirji. Ali ya ƙaraso yana haɗe fuska "Maryam idan ba za ki buɗe mini ba na koma inda na fito!". Ya faɗa ganin ba ta da niyyar buɗe gidan tana binsa da kallo, ta girgiza kai ta buɗe sai da ya shiga sannan ta bi bayansa ta saka sakata, cike da mita yake cewa"Wannan wane irin hali ne, ki dinga cewa kina jin tsoron zama ke kaɗai, saboda tsabar raini sai ki fito ƙofar gida ki tsaya masu wucewa suna kallonki kina kallonsu wannan ai raini ne!". Maryam tana cire hijjabi ta ce"Duk yadda ka ɗauka, ni dai ba zai taɓa yiwuwa ka fita tun safe sai dare ba kuma ace daren ma wai ba ka da lokacina sai ka gama fira a majalisa, ka ɗakko ni a gidanmu mai cike da jama'a ana raha ana dariya ka zo nan ka kulle ni kai kana majalisa? Kar ka ga ina tsayawa a ƙofar gida, wallahi duk ranar da ka yi sake na gano majalisar nan taku sai dai a fara zaman da ni..." Ransa ya ɓaci ya ce"To bisimillah ai ga hanya nan, wallahi Hamza sai ya kai sha biyu a waje, amma dayake shi yana da ƴanci matarsa ko waya ba ta isa ta yi masa ba, ke da nake dawowa takwas da rabi ba za ki godewa Allah ba?" Ta taɓe baki ta ce"Ita ta ga za ta iya, don ni wallahi duk ranar da ka kai ƙarfe goma a waje ka saka a ranka babu kai babu kwana a gidanka, don wallahi tabarma zan kai maka shago kafin ka dawo!". Daga haka ta fita ta ɗauki bokiti ta zuba masa ruwan wanka ta kai masa banɗaki tana ci gaba da mita "Ni an isa a dawo min gida sha biyu, sai ka ce ƴar iska mutum ya ajiye? Tab". Kafin ya fito daga wanka ta kawo abinci falon, ta zuba musu, suna gamawa nefa suna kawo wuta, ta ɗauki wayarta ta jona, za ta ɗauki tashi ya ce ta bar shi yana da caji, ta kunna kallo a ƙaramar tv dake falon, tana kuma jansa da fira yana mazewa, ganin hankalinsa ba ya kanta ya sa ta tattara hankalinta kan tv. Shi kuwa Aliyyu jinsa yake tamkar a kan ƙaya, hankalinsa sam ba ya gidan da yake a zaune, fargaba ce fal zuciyarsa, saboda sanin halin Reza wacce ya karya mata alƙawarin haɗuwar da za su yi yau don ya ba ta rabin kuɗinta ya kuma ba ta haƙuri kan sauran kuɗin, amma saboda sanin halin Maryam dole ya haƙura ya dawo gida, wayar ya ɗauka ya saka a silent, babu jimawa kuwa sai ga kira yana dubawa ya ga Rezar ce, gabansa ya faɗi, ya ɗan tura wayar ƙarƙashin kujera, amma hankalinsa yana kanta yana ta ganin haske na kawowa yana ɗaukewa, sai jan tsaki yake cike da fargabar furucin Rezar na cewa yau har gidansa sai ta zo akan kuɗinta. Maryam wacce tsakin ya fara ba ta mamaki, ta juyo tana haɗe gira ta ce"Wai ni kam Love tsakin me kakr ta jerowa ne? Na lura tun da ka dawo ba ka da nutsuwa". Ya sauke numfashi ya ce"Wallahi Love mantawa na yi ban siyo biredi ba, shi ne duk abin ya dame ni". Lokaci ɗaya ta haɗe rai, don ta san indai ya fita siyan biredin nan fa sai an gan shi, ta ce"Ka bar shi kawai, a dafa indomi". Ya ce"Ai kuma shayin nake son karyawa da shi, wallahi minti biyar ya yi yawa, kin ji?" Ta juya kai ba ta ce komai ba, hakan ya sa ya gane ta yarda ya fita amma ba da son ranta ba. Ya tashi zai fita, ta ce"Ara min wayarka". Ƙirjinsa ya buga, ya ce"Ai fa yau ƙaraf na dawo gidan, transfer zan yi wa mai biredin". Ya fice yana jin salama a ransa, sai da ya yi nisa da gidan sannan ya kira lambar Reza, tana ɗagawa ta fara masifa"Wai kai Ali ni za ka rainawa hankali saboda ka yi aure ko? To idan ban kashe auren ba Allah Ya..." Kafin ta ƙarasa ya katse ta da faɗin"Subhanallah! Haba Reza, ke me yasa ba ki da uzuri? A ina za mu haɗu?" Tana faɗa masa gidanta zai kai mata ya kama hanya jiki na rawa saboda da ɗan nisa, kamar zai yi kuka saboda takaicin fitar da kuɗin ya ba ta dubu biyar yana ba ta haƙurin gobe zai cika mata dubu biyar, duk da ya san ba zai taɓa yiwuwa ya bata a goben ba, don wannan biyar ɗin ma da ƙyar ya haɗa ta, ya bar gidan zuciyarsa fal ƙunci, a hanya ya tsaya ya sayi biredin ya koma gida da ƴar fargaba. Har ta yi bacci saboda an ɗauke wuta kuma ya daɗe, ya ɗauki radionsa dake kan mudubi, ya haska ta a ransa yana cewa'fitinanniyar yarinya', sosai yake jin daɗin saurin baccinta, saboda daren ne kawai yake da lokacin wayarsa inda yake cin karensa babu babbaka da ƴan matansa, falo ya koma ya kwanta ya kunna radion ya ajiye, don haka yake yi idan Maryam za ta takura masa kan ya zo su kwanta, sai ya ce shiri yake ji, ko ta yi zaman jiransa jin radion ba ya ƙarewa, sai ta haƙura ta je ta kwanta. Data ya kunna ya shiga chart da Baby Farha wacce jiya suka haɗu da ita a wani group ɗinsu mai suna ƴan hutu, sosai jiya ya ji daɗin haɗuwarsa da ita kuma daga ganin hotonta ƴar hutun ce da gaske, saboda haka bai yi ƙasa a gwiwa ba ya shiga sharara mata ƙarya da nuna shi ma ɗan hutun ne kuma babban ɗan kasuwa, suna ta fira idan zai yi mata voice sai ya kashe radionsa ya narke murya yana iyayi kamar mace, shi a dole ɗan hutu. Sai ƙarfe ɗaya Maryam ta farka, yana jin ƙarar ɗaukar buta ta shiga banɗaki, ya yi maza ya kashe wayar duka ya baje a ƙasan kafet yana jan munshari. Ta leƙo ta haska shi tana mai jin tausayinsa, ta san a gajiye yake saboda yanayin aikinsa na kafinta, ga shi wuni yake a can, ta kira sa da 'Love' Ya tashi a firgice yana mirtsika ido ya ce"A...wai bacci na yi a nan? Ikon Allah kin ga fa radio nake ji ashe bacci ya ci ƙarfina". Ya kashe radion da ke ta shuuuu don tuni sun rufe gidan radio, ya kulle falon. Kafin ya shiga ɗakin gadon har ta kwanta, ta baje don ci gaba da baccinta, a hankali ya kai hannunsa jikinta, wanda ta ji saukar hannun kamar saukar wuta a jikinta, idan da abin da ta tsana a aure to wannan fannin ne, tsam ta cire hannunsa daga jikinta ta ce"Don Allah ka yi haƙuri, wai sau nawa zan faɗa maka duk wani abu da ya biyo bayan bacci haramun ne?". "Hmm!" Ya sauke ajiyar zuciya, yana matsawa gefe, don shi dai ba wani zurfi ya yi a islamiyya ba, ganin ita kuma ta yi karatun ya sa shi zaton wannan hadisi ne, cewar ba a tashin mace a neme ta idan ta riga ta yi bacci, ajiyar zuciya ya sauke, ya juya mata baya, a zuciyarsa yana ta hango surar Baby Farha wacce yake so yana samun wasu kuɗi da yake jira ya ziyarce ta, idan Allah Ya taimake shi ƴar hannu ce sai ya san yadda zai ɓullo mata. GIDAN SADIQ Riƙe yake da hannun ƴaƴan nasa biyu mata wanda ya karɓo su daga maƙota, Afna har ta fara bacci aka tashe ta, ita ma Fanan daga gani baccin ne a idonta, ya buɗe gidan suka shiga zuciyarsa sam babu daɗi, kaca-kaca ya tarar da falon, ya yi ƙwafa ya kalli yaran ya ce"Kun ci abinci?" Suka girgiza masa kai alamar ba su ci ba, ya shiga kitchen, nan ma ya tarar da wanke-wanke a zube, nan ya duba kuloli da tukwane ya fahimci ba ta yi girki ba ta fita, idan da sabo ya saba da yin girki, don haka ya kunna gas sai ya ga ashe ya ƙare, tsaki ya yi ya ɗakko flas ya ga wayam babu ruwan zafin ma"Allah na gode maka!" Ya faɗa yana buɗe wani ɗan bokiti ya ɗauki plate ya zuba cake ɗin da ke ciki, ya dawo falo ya buɗe firji ya ɗakko lemo ya zauna yana janyo yaran jikinsa, ganin duk sun noƙe yasa shi ƙirƙirar murmushi ya ce"Ku zo mu ci ko". Fanan da ita ce babba ta ɓata fuska ta ce"Daddy da rana ma fa shi muka ci, da safe ma da shi muka je makaranta, kuma ma Afna ba ta so, ni ma ya ishe ni". Ya sauke ajiyar zuciya ya ce"Ku yi haƙuri ƙawayena ku ci kun ji? Babu kyau kwanciya da yunwa". Da ƙyar ya lallaɓa su, Fanan ta ci, ita kuwa Afna sai shayi ya haɗa mata da ruwan sanyi, shi ma tun safe babu komai a cikinsa, don haka ya ci cake ɗin, yana son duba littafansu ko da home work amma ya san bacci suke ji, ya yi musu shimfiɗa a ɗakinsu ya kwanta a ƙasa su suna gado, bayan ya yi musu addu'a sun fara bacci, ya janyo wayarsa ya kira lambar mahaifiyarsu. "Hello Masoyi sorry yanzu nake shirin kiranka". Ta faɗa ta cikin wayar cike da kulawa. Jin ya yi shiru ya sa ta sake cewa"Ina yaran, ka dawo gida?" Ya ce"Yusra me yasa gas ya ƙare ba ki faɗa min ba?" Ta ce"Oh my God! Wallahi na manta, na so ma na aiko Nura ya ɗauka sai na sha'afa". Ya ce"Amma me kike yi tun da rana a gidan?" Cike da gajiyawa ta ce"Oh! Yau fa na zauna sosai a kemis, kuma na je wani gida karɓar haihuwa, sai magriba ma na shiga asibiti a latti". "Ok sai da safe" Ya faɗa yana shirin katse kiran. Ta ce"Na gode Masoyi". Ya ajiye wayar yana tunanin kalar rayuwar gidan nasa, da haka bacci ya kwashe shi, yana dawowa daga sallar asuba ya ɗora musu abin karyawa a electric kasancewa akwai nefa, shi ya shirya yaran suka ci abinci ya saka musu wanda za su tafi da shi, ya bar mata nata, ya jira mai mashin ya zo ya tafi da su makaranta, shi ma ya tafi shagonsa na provition da babu nisa da gidansa. Bakwai da rabi Yusra ta koma gida, don ta tsaya jiran wacce za ta karɓi dutyn safe, saboda tana bawa wata mai naƙuda kulawa sosai, ba ta so ta barta sai ta damƙa ta a hannun wacce ta san za ta kula da ita, duk saurinta ba ta tarar da su a gidan ba, bacci ne fal idonta amma haka ta haƙura tana ajiye jaka ta shiga kitchen ta fara wanke-wanke, sai da ta gyara ko'ina gidan ya dawo hayyacinsa ya ɗauki ƙamshi sannan ta ci abincin da ya ajiye mata, ta yi wanka ta ɗauki waya ta kira shi, "Ina kwana?" Ta gaishe shi bayan ya ɗauki wayar. "Kin dawo?" Ya tambaya ba tare da ya amsa gaisuwar ba. Ta ce"Na dawo". "Ok anjima kaɗan zan kawo cefane". Ya faɗa yana sauke numfashin da ta san fassarsa. Ta ce"Ka bar shi, wake da shinkafa zan yi ai, kuma Nura zai zubo gas". "Zan zo dai" Ya faɗa. Ta ce"Masoyi da ka haƙura dai, wallahi jiya ban samu bacci ba, yanzu ina dawowa na hau kan aikin gida, bacci zan yi kafin na tashi ɗora girkin rana, kaina har ciwo yake". Yana haɗiye ɓacin ransa ya ce"Amma yau ma fa dutyn dare za ki fita, ba kya tunanin..." Ta katse shi da faɗin"Don Allah Masoyi, gobe ina gida fa". "Ok" Ya faɗa, yana katse kiran. Ita kuma ta gyara kwanciyarta ta fara bacci hankali kwance. Sai sha biyu ta tashi, ta kira yaronta Nura ya sako mata gas, har ma da cefanen kayan miya, don ba ta son zuwan mijinta shi yasa ta ce masa ba sai ya kawo cefane ba, saboda ta san idan ya zo hana ta bacci kawai zai yi, shi ma ya katsewa kansa kasuwa, a gurguje ta yi shinkafa da miya, tana saukewa ta ɗora tuwon dare don shi a son samunsa kullum ya ci tuwo da daddare, amma ba kullum take samun damar yi masa ba, saboda aiki, ƙarfe ɗaya aka dawo da yaran daga makaranta, suka ci abinci ta yi musu wanka, sai da suka saka unifom ɗin islamiyya sannan ta fito da littafansu suka yi home work, tana sauke tuwo ta yi wanka, ta shirya ta ɗauki abincin Sadiq ta haɗa kansu ta kai su makarantar da babu nisa da gidansu, sannan ta wuce shagonsa don kai masa abincin. Gefe ta tsaya sai da na ciki suka fita, sannan ta ƙarasa murmushi ɗauke a kan fuskarta ta ce"Sannu da aiki Masoyi". Ya yi guntun murmushi yana kallon yadda ta yi kyau tana zuba ƙamshi duk da ba kwalliya ta yi ba ya ce"Na gode". Ta ajiye masa kular tana cewa"Ya kake, komai ƙalau ko?" Ya gyaɗa mata kai yana ta kallonta. "Kemis?" Ya tambaye ta. Ta gyaɗa kai ta ce"E zan je na ɗan zauna, na gama aikin gidan, har tuwo na yi maka". Ya ce"Kin kyauta kuwa, sai goben". Ta yi murmushi ta fice, yaran sun sani daga islamiyya maƙotansu za su shiga, sai ya dawo bayan sallar isha'i ya ɗakko su, duk da ranar da ba ta nan ne yake katse kasuwar, amma a ƙa'ida goma da rabi yake tashi. GIDAN HARUNA Ƙarar alarm ne ya karaɗe ɗakin, hakan ya sa Halima tashi a firgice, ta janyo wayar da ke kusa da ita ta latsa alarm ɗin ya mutu, bakinta ɗauke da addu'ar tashi daga bacci ta miƙe zaune, ta dafe kanta tana jin yadda ya sara mata, tun dare ta kwanta da ciwon kan, ga shi har yanzu bai sauka ba, sakkowa ta yi daga gadon ta fita tayo alwala ta dawo ta canza kaya ta kabbara sallar da ake yi ta asuba, tana lazimi tana gyangyaɗi har bacci mai ɗan nauyi ya kwashe ta daga zaunen, a firgice ta tashi ta ga gari har ya yi haske, ga kukan tsuntsayen da suke faɗa mata lokaci ko da babu agogo, da sauri ta fita ta kunna murhunta na gawayi, sannan ta dawo ɗaki ta fara firfito da kayan sana'arta ta wainar fulawa, wata matashiya ce ta fito daga ɗakin dake kusa da nata tana cewa"Ashe kin fito, yanzu nake cewa yau Halima ta makara". Halima ta yi murmushi ta ce"Zainab ina kwana? Wallahi yau baccin ya yi mini nauyi ga ciwon kai tun jiya". Zainab ta ce"Ai ke ce ba kya hutawa Halima, sai ki sha magani kafin ki hau suyar nan". Jin ba ta bata amsa ba ya sa ta san ba ta da maganin, ta shiga ɗaki ta fito hannunta ɗauke da kofi da kuma maganin, kunun alkama da ta saba damawa ne ta miƙawa Halima tare da maganin, ta karɓa tana godiya, ta kwankwaɗe sannan ta sha maganin, Zainab ta ce"Zauna ya ɗan tsarga miki Halima bari na fifita miki wutar". Ba don kan ya daina ciwo ba ta tashi ta hau suyar wainar, mutane suna ta shigowa suna siya, yawancinsu ƴan makaranta ne, sai da ta gama tsaf sannan ta saka a farantai biyu ta miƙawa Zainab ta leƙa ɗakin da Zainab ɗin ta fito wanda kakarta ke ciki tana jin radio ta miƙa mata, suna gaisawa. Ta dafa shayi ta juye a flas ta ɗauki wainar da ta zuba a wata ƴar kula ta kai ɗaki ta ajiye, tana nan zaune a tsakar gida tana wanke-wanke yaron da yake kai mata tallar wainar makaranta ya zo ya ɗauka ya tafi, bayan ta share tsakar gida ta shiga ɗaki ta auno shinkafar da take dafawa ta siyarwa ta fito ta fara tsince ta, sai da ta gama ta ɗora tukunya ta saka wake, sannan ta koma ɗaki ta tarar mijinta ya tashi, ta kalle shi cike da takaici ko sallar asuba bai yi ba, sai yanzu zai yi idan har an yi sa'a yana da niyyar yi a ranar, ta kalli yadda daga tashinsa har ya ɗauki waya duk da ta san halayyarsa ce amma tana takaicin abun. "Ga wainarka da shayi" Ta faɗa tana tura kayan gabansa Ya ce"Ki ɗan dafa min taliya da ita zan karya, wannan wainar kuma ki samu leda ki saka min". Ta ce"Taliya ai ka san ta ƙare". Ya yi tsaki ya tashi ya fita don yin wanka, daga shi sai gajeren wando, wanda har zuciyarta ba ta son hakan, ko don Zainab da ke zaune a tsakar gidan kullum daidai wannan lokacin, ta yi masa ƙorafi har ta gaji, ta lura abun ya bi jikinsa ne. Yana gama karyawa ya fara sosa kai, tsaki ya ja fuskarsa ta nuna alamun damuwa, Halima da ta san kwanan zancen ta ce"Lafiya kake tsaki?" Haruna ya ce"Wallahi Halima jiya zero na shigo gidan nan, wannan shinkafar ma bashi na karɓo ta, kin ga bai kamata yanzu na fita ban bar miki komai ba". Ta yi guntun murmushi ta ce"Haba kar ka damu, Allah zai rufa asiri, watarana sai labari, ga wannan ka hau babur". Ta ƙarasa tana miƙa masa ɗari biyu Ya karɓa ya ce"Na gode, kai ni kam na yi sa'ar mace ta gari, Allah Ya shi miki albarka". Ta amsa da amin, shi kuma ya fice. Ta yi shiru tana tunanin kalar rayuwar auren da take yi, sam Haruna ba shi da zuciyar nema, dududu wata uku kenan da auren amma kullum a haka ake, dama a wurin da take siyar da abinci suka haɗu har ya aure ta, don haka da ta lura da irin mijin da ƙaddara ta zaɓo mata, sai ta fara sana'o'inta, tun da idan ya kawo abin da za a dafa shi kenan, babu ruwansa da mahaɗi, ita ce gawayi, mai, magi, kayan miya, omo, sabulu da siyan ruwa, sai dai duk ranar da ya samu yana ba ta dubu ɗaya, saboda haka take ƙara dagewa a kan neman na kanta don ta rufawa kanta asiri. A zaure suka yi kiciɓus da Zainab ta sha gabansa tana cewa"Haruna ni me kake nufi da ni wai? Jiya ko biyar ba ka ba ni ba yau ma..?" Tana direwa ya ce"Ki yi haƙuri Zee, wallahi jiya ban shigo da komai ba, shi yasa ma kika ga na yi dare, saboda shinkafa ma a tata na ɗiba na saka a leda na ajiye kawai, saboda ta yi zaton da ita na shigo, amma yau dole zan shigo miki da wani abu, ai za mu haɗu ko tawan?" Ta ruƙo hannunsa ta ce"Ko na karyawa fa ba ni da shi". Ya sauke numfashi cikin sarewa da halinta, ya ciro ɗari biyun da Halima ta ba shi ya ba ta, ya fice. Ta soke a hularta, ta shigo gidan tana gyara rigarta da ta zame ta don ta ɗauki hankalinsa, ta shigo ta fara fifitawa Halima wuta tana ɗan ɗaga murya ta ce"Halima fito da barkonon na daka miki". Tana murmushi ta fito da shi, a ranta tana jin daɗin irin kirkin Zainab da kakarta wanda yau satinsu uku kenan da tarewa a gidan, amma har sun saba. 08028966015 [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS PAGE 2 Da ƙyar Maryam ta iya tashin Ali ya tafi masallaci sallar asuba, saboda nauyin da bacci yake yi masa, amma da ya idar da sallah sai da ya zauna a masallacin ya kunna data, ya dudduba saƙonni, lambar Baby Farha ya duba ya ga ba ta hau online ba, ya yi murmushi yana ayyana tana can tana bacci a cikin AC. Lokacin da ya dawo tana zaune a sallayar da ta idar da sallah, ya kwanta yana jira ta gama ita ma ta zo ta kwanta, ganin shiru ba ta da niyyar tashi ya sa shi cewa"Love me kike yi ne? Jiranki fa nake" Nan take ta haɗe rai, dama ta san kwanan zancen shiyasa ta zaɓi ta yi zamanta har gari ya yi haske ta fita ta dafa shayi, sai ga shi dai ba ta tsira ba, ita kam tana son mijinta, tana kishinsa sosai, amma ta tsani ya neme ta a shimfiɗa, wannan shi ne babbar matsalarta, a zatonta rashin sabo ne da farko amma yanzu ga shi har auren ya yi wata shida a haka ake, ta sani ba ta ba shi haƙƙinsa yadda ya kamata, kawai yana ƙyale ta ne saboda a zauna lafiya kuma ta san yana shakkarta, hakan kuwa ya samo asali ne ta yadda yake bala'in sonta, sannan ya kasa maza da dama kafin ya same ta, ciki kuwa har da waɗanda suka fi shi komai na rayuwa, a lokacin an zuga Maryam sosai a kan aurensu, masu rufin asiri suna sonta amma za ta auri kafinta wanda zai kai ta gidan haya, ta ce ita ta ji ta gani. "Ko ba zan samu ba?" Ya tambaye ta yana karaya da lamarinta, shi mutum ne mai ƙarfin sha'awa, wanda har yake ganin hakan shi ne ƙaddararsa, don tun da ya fara sana'a yake samun na kashewa ya fara neman mata bisa shawarar abokai, a yadda suke faɗa masa, ai shi saurayi ne ko a shari'a idan an kama shi ma bulala ce kawai, kuma yana yin aure zai daina, hakan ne ma ya sa shi dagewa ya yi auren don ya samu cikakkiyar nutsuwa da halalinsa, sai kuma Allah Ya haɗa shi da mace mai gudunsa, sosai abun yake ci masa tuwo a ƙwarya, don haka ya kasa yakice wa kansa wannan halayar, ko chart ɗin batsa duk yana yi ne saboda ragewa kansa damuwar nan da kuma sabo. Haka dai ta je gare shi ranta babu daɗi, kuma ya san yau a haka za ta wuni da ƙuncin nan, shi yasa idan aljihunsa da nauyi yake gwammacewa ya tafi wurin matan banza inda za a faranta masa ya biya, a haka ne har bashin dubu goma ya shiga tsakaninsa da Reza, wanda ba dan haka ba da dubu biyar ɗin da ya ba ta jiya sai dai ya yi musu buƙatun cikin gida, ita kuwa ƙarya da yake yi wa ƴan mata a waya dama halinsa ne, ba ma zai taɓa iya dainawa ba. Suna gama karyawa ya tafi aiki, ita kuma ta shiga harkokinta na cikin gida, tun tana gida sana'arta ce kitso da ƙunshi kuma har yanzun ma tana yi ba ta watsar ba, gidan nata ba ya rabo da mata, maƙotanta masu sana'a ma duk nan ne majalisarsu, ana kitso ana kitsa gulma, don ma dai ana shakkarta don ba ta da wasa, sai dai ko ba ta gama ba magriba tana yi ta rufe sana'a, ta gyara gida ta ɗora girki sannan ta yi wanka ta yi kwalliya, ta jira dawowar mijinta, idan da abin da ta tsana bai wuce duhu ya yi ta ganta ita kaɗai ba, da ƙyar ta amince da cewar sai takwas da rabi zai dinga dawowa gida, kuma tana gotawa za ta fara mita tana kiransa a waya, idan ta gaji sai ta rufe gidan ta jira shi a ƙofar gida. Yau ma kamar kullum, ta gama komai ta idar da sallar isha'i, ta kame tana jiran dawowarsa. Tun da Ali ya fita da safe, wajen aikinsa ya wuce, ya shiga aiki tuƙuru, babu zancen kula kira da plashing ɗin da ƴan mata suke yi masa, yawanci waɗanda ba su daɗe da haɗuwa ba ne suke kiransa, amma duk wacce suka daɗe ta san da cewa Aliyyu ba ya haɗa aikinsa da komai, idan yana office ba ya ɗaukar wayarsa sai ya fito, da haka yake neman na kanshi domin ya samu asirinsa ya rufu, wajen aikin babu nisa da gidan iyayensa, a nan yake zuwa ya ci abincin rana ko a aiko masa, sai magriba ya tashi daga aiki, sallah ya yi ya shiga gidansu suka taɓa fira da ƴan'uwa, sannan ya tafi majalisar unguwar bai jima da zama ba Reza ta kira shi, ya ɗauki wayar kamar zai yi kuka ya ce"Reza idan kin yi haƙuri ma ai zan kira ki". Ta ce"To ina jiranka...". Ya katse ta da faɗin"Ki ƙara min haƙuri don Allah, wallahi ba su samu ba, sai dai ko gobe". Ta ce"Ali kar fa ka mai da ni ƴar iska". Ya yi dariya ya ce"To da mece ce?" Ta ce"Dariya ma kake yi kenan! Wallahi idan ban zo gidanka na tona maka asiri ba shegiya ce ni, ɗan iska ka yi auren ma ba ka daina cin bashi ba". Ali ya ce"Ni dai ki yi haƙuri, tsautsayi ne ya ja ni, da ba ki zage ni ba". Ta ce"Ka nemi kuɗina ka ba ni". Ya ce"Gobe zan kawo miki in sha Allah!" Suka ajiye waya. Ya fito daga sallar isha'i kenan sai ga kiran Maryam, yana ɗauka ta ce"Na ji shiru, wallahi yunwa nake ji yau, don Allah ka dawo da wuri". Bai ce komai ba ya kashe wayar, ya buga babur ɗinsa, abokansa suna ta yi masa tsiya, Madam ta yi kira, shi dai ya ɗauki hanyar tafiya gida, yana takaicin yadda take kafa masa takunkumin nan, sai ta ce ba ta iya cin abinci ita kaɗai, kuma ta yi ta kiransa tana ce masa yunwa take ji, ya dawo su ci. Tana zaune tana kallo a waya ya same ta, ta yi masa sannu, ta kai masa ruwa ya yi wanka, sannan ta kawo musu abinci, suna cikin ci sai ga kira a wayarsa, sai da gabansa ya faɗi saboda harƙallar rashin gaskiya da yake yi, indai aka kira shi a gaban Maryam sai ya ji faɗuwar gaban nan, da ya ga abokinsa Hamza ne mai kiran sai ya ji dama-dama, ya ɗaga yana cewa"Hamza ya ne?" Daga can ɓangaren Hamza ya ce"Wallahi aboki wani kaya ne mai zafi ya samu, sai ka gani dai ka fito muna bayan layinku". Ƙirjinsa ya ba da rass, ya kalli Maryam wacce ta dakata da cin abincin ta kafe shi da ido, don duk a abokansa ta fi tsanar wannan Hamzan, tun da ta lura ya fi maƙale masa, kuma tana jin sautin wayar ta ji ana magana da kurman baƙi, ta fara tunanin wane kaya ne me zafi mijinta zai siya? Tsam ya tashi zai fita, yana hello hello, alamar babu network, bai ankara ba ya ga Maryam ta ruƙo rigarsa ta zaunar da shi, ta yi masa nuni da abincin dake gabansu. Cikin karaya ya ce"Hamza wai katakon ne aka samu masu kyau?" Hamza ya ce"Kai dalla Malam ina yi maka zancen kaya kana ce min katako, wata mai zafi aka samu fa, kuma wallahi babu tsada..." Da sauri Ali ya katse shi da faɗin"Au shadda? Ai sai ka ce min wannan shaddar da zan siya wa Maryam an samu, ka tsaya kwana-kwana?" Hamza ya ce"Kana gida ne?" Ali ya ce"Ina gida, amma ka ajiye min gobe za mu yi magana, duk da ba ni da kuɗin ma". Suka yi sallama, ya kalli Maryam yana sauke ajiyar zuciya, suka ci gaba da cin abincin tana auna maganganunsu a zuciyarta. Yau ma dai gajiya ta yi da ƙarar radionsa ta je ta kwanta, hakan ya ba shi damar dulmiya duniyar wayarsa, ya yi mamaki da har Baby Farha ta fara yi masa zancen yaushe zai je gidansu? Hakan ya ba shi tabbacin ba ƴar ƙarya ba ce, don ƴan ƙarya yana cewa zai je suke kawo masa uzuri har a bar zancen, ya faɗa mata zai zo cikin satin, sai kuma ya fara tunanin kayan da zai saka, don hotunan da ya tura mata sun kwana biyu, yanzu kayan sun sha wanki, ya fara tunanin dole nan gaba ya fara aron kayan sakawa kafin ya ɗinka sababbi, da wannan tunanin ya yi bacci, bayan ya gama tashin kan ƴan mata da ƙarya. GIDAN SADIQ Yau tun magriba ya rufe shagon, ya je ya kwaso ƴaƴansa, saboda ba ya son barinsu a maƙotan nan don dai babu yadda zai yi ne kawai, gida suka shiga ya canza musu kaya, ya wanke unifom ɗin, sannan ya saka musu tuwo, shi ma ya saka, suna gamawa ya ɗakko littafansu babu home work sai ya yi musu bitar karatu, ya kunna musu surar da suke a islamiyya, suna saurara har bacci ya ɗauke su, a gida ya yi sallar isha'i, ya yi musu shimfiɗa suka kwanta ya tofe su da addu'a, sannan ya kira lambar Yusra har sau uku ba ta ɗauka ba, tun jiya yake cikin yanayi na buƙatuwa, amma babu yadda zai yi kamar dai gwauro, sau da yawa yakan yi tunanin duba shawararwarin da mahaifiyarsa take ba shi akan aikin Yusra, ko dai ya mata tilas ta ajiye ta kula da gidanta, ko shi ya ƙara aure, amma idan ya tuna yadda take da kishi sai ya kau da zancen, saboda yana ƙaunarta, ba ya son abin da zai kawo rabuwar kai a tsakaninsu, duk da ya san ba za a taɓa dawwama a haka ba, don hanyar da gidansa ta ɗakko ba mai ɓillewa ba ce, da wannan tunanin bacci ya ɗauke shi. Sai wajen sha ɗaya ya ji ringin ɗin wayarsa ya duba ya ga ita ce, kamar ya share sai kuma ya ɗaga don wataran takan dawo cikin daren ta ce ta gudo, jin tana tambayarsa ya gidan yara sun yi bacci? Kawai sai ya kashe wayar ma duka ya ci gaba da baccinsa. Da safe shayi ya dafa musu da ɗumamen tuwo, ya yi musu wanka ya shirya su suka tafi makaranta, shi ma ya tafi shago. Tana dawowa ta gyara gida, ta sha sauran shayin da biredi, ta yi wanka ta zauna har za ta kira wayarsa ta fasa, don kar ma ya ce zai zo, ta yi kwanciyarta, da wuri ta yi girki, ta zuba na yara ta kai musu maƙota, sannan ta zuba na shi ta bawa yaro ya kai masa, ta zuba nata a kula ta tafi kemis, daga nan ta wuce asibiti. Yau dab da magriba ta dawo, kusan lokaci ɗaya da yaranta, ta shiga ta taho da su, suna ta farin cikin yau Momynsu tana gida, sosai suke kewarta idan tana yin aikin kwana, don ma wani lokacin tana zuwa har islamiyyar ta gansu, cike da farin ciki suke ta ba ta labarin makaranta, su suka zaɓi abincin da za a dafa, ta ɗora, suka yi sallah tare, sannan ta yi musu wanka, tana taya su home work har ta gama girkin, suka ci a faranti ɗaya cike da ƙauna irin ta uwa da ƴaƴanta, bayan sun gama ta ba su wayarta suna ta kallon bidiyoyin yara na ilimi har suka yi bacci, ta gyara shimfiɗa ta kwantar da su, sannan ta yi wanka ta shirya cikin kayan bacci. Tana kwance tana ɗan taɓa chatting ya dawo, wajen tara da rabi, ta je ta karɓi ledar hannunsa tana yi masa murmushi mai cike da ƙauna, ta kai kitchen ta taho da abincinsa, kafin ta fito har ya shiga wanka, a bakin gado ta zauna ta ɗauki wayarsa da ke ajiye, wacce ta san babu ruwan shi da saka cord, ta duba call long ta yi murmushi ganin duk amintattun kira ne babu na zargi, haka ma massages, shi babu ruwansa da chart, babu ma App ɗin whatsApp a wayar, sai facebook da yake da tsirarun abokai, wannan tana yawan dubawa ta wayarta don ta ga abokansa, tun da nan ma bai wani saka tsaro ba. Tana ajiye wayar yana fitowa daga banɗakin, ta sakar masa murmushi, ya yi mata murmushin gefen baki, jikinta ya ɗan yi sanyi, don ba haka suka saba ba, a hankali ta ƙarasa inda yake tsaye a gaban sif yana duba kayan da zai saka, gabansa ta je ta tsaya ta riƙe duka hannuwansa daga ɗaukar kayan, ta shiga jikinsa ta kwanta, ya shafa kanta bai ce komai ba, ta ce"Na ga kamar kana cikin damuwa". Kai tsaye ya ce"Ai ke ce". Ta ce"To ka yi haƙuri, yanzu ba ga ni ba?" Ya ja hannunta zuwa gadon, tana ta narke masa, har suka samu nutsuwa cike da ƙaunar juna, sun yi wanka sun fito suna cin abinci ta lura da yadda har lokacin ba ya cikin shauki kamar da, ta tattara hankalinta gare shi ta ce"Masoyi akwai abin da yake damunka bayan kewata, don Allah kar ka ɓoye mini". Ya yi saurin girgiza kai, ya ce"Babu komai Masoyiya yanayi ne kawai, kwana biyu kamar zan yi zazzaɓi, kuma kewarki ce take haddasa mini irin hakan, ina da mata amma na kwana da kewa kamar mara gata...". Ta katse shi a shagwaɓe ta ce"Don Allah kar ka ce haka, yanzu ba ga shi kewa ta tafi ba?" Ya ce"Amma haka zan rayu ba kodayaushe zan samu kulawarki ba?" Ta ce"Ka yi haƙuri don Allah, yanayi ne ya zo da haka". Ya ce"Amma idan na ce miki yanayi ya saka ni son ƙara aure za ki fahimta?" "Sadiq! Aure za ka yi?" Ta tambaye shi a tsorace Ya girgiza kai ya ce"Sam, kawai tambayarki na yi". Jiki a sanyaye ta ce"Wannan bai kai dalilin ƙara aure ba, kuma ma na ga..." "Ya isa, gwada ki na yi fa" Ya katse ta. Ta sauke ajiyar zuciya ta yi murmushi ba don ta yarda da cewar gwajin ba ne, da wannan tunanin ta kwana a ranta. GIDAN HARUNA Kasuwa Haruna ya nufa kai tsaye, don yaron shago ne, kasancewar babban shago ne ana biyansa daidai gwargwado, sai dai wannan halayyar tasa da ta zame masa katankatana ita ce take lamushe duk wani abu da zai samu, duk a zatonsa idan ya yi aure shi kenan matsala ta mutu, da farko kamar gaske sai daga baya ya ji ya rage samun nutsuwa da Halima, sannan ma sam ba ta da wayewa ta wannan fannin, ta ƙi sakin jiki da shi, su na bazan sun fi ta iya komai da yake so, shi yasa ya fi samun nutsuwa da su. A duk inda ɗan bariki ya haɗu da ɗan'uwansa ba ya ɓuya, don haka tun a satin farko da su Zainab suka tare a gidan ya gane ita ma ƴar hannu ce, kamar da wasa wataran zai shiga wanka tana zaune ya tsaya yana kallonta, sai ya ga ta ɗage masa gira tana kashe ido, ya yi murmushin jin daɗi don tun a ranar farko da ya fara ganinta ya kwaɗaita da ita, bayan an kwana biyu yana ƙofar gida ta zo za ta shiga kawai ta shafa bayansa za ta shige, ya taso da sauri yana miƙa mata wayarsa, ta saka masa lambarta, kuma tana shiga gida ya kira ta, su ka yi ta waya kamar sun saba, daga nan suka fara chart na musayar kalaman banza don kar ta san kar babu wani abun ɓata lokaci, sautari idan zai shigo gida yakan taho mata da leda tsire ko balangu ko dangin kayan sanyi, kafin ya ƙaraso sai ya yi mata waya ta same shi a zaure, ya lalube jikinta ta karɓi leda ta shige gida, sannan shi ma ya shiga kamar ba a yi komai ba, duk ranar da bai taho mata da komai ba ba ya faɗa mata ga shi nan zai shigo, ita kuma da safe sai ta daidaici fitarsa sun haɗu a zaure, don tana da mugun son banza, irin matan nan ne ma su yi wa maza kankat idan suka shiga komarsu. Yau ma hakan ce ta faru, ya samu alheri a kasuwa babu laifi, don haka ya ƙunso mata balangu mai zafi da yogurt, ya sayi taliya leda uku, sabulun wanka da omon wanki, don ya ragewa Halima. A zaure ya tsaya ya kira ta ba ta ɗaga ba, don lokacin tana tsakar gida wayar tana ɗaki, tana ganinsa ta taho da sauri za ta rungume shi, ya kauce yana kallon ɗakinsa ya ce"Haba Zee mene ne haka?" "Naki yana zaure" Ya faɗa yana saurin shigewa ɗaki. Ita kuma ta je ta ɗakko ledar ta shiga ɗaki, ta baje ledar cike da zumuɗi, Baaba ta ƙure ta da kallo ta ce"Ke Zainab a ina kike samo balangun nan ne?" Ta haɗe gira ta ce"Haba Baaba ai kin san saurayina ne yake kawo min". Baaba ta ce"To me yasa ba kwa zancen ne sai dai ki leƙa ki karɓo ya tafi?" Ta ce"Aiki ne yake yi masa yawa wallahi, kuma shi dayake aure ne a gabansa ba ya son ma dogon zance, sai ya ce duk ƙarya ce ake shararawa". Baaba ta sauke ajiyar zuciya tana karɓar balangun da Zainab ta ɗibar mata ta ce"Ni dai don Allah ki kama kanki Zainab, kin ga dai amana na karɓa, ki taimake ni na aurar da ke kar ki sake jajibo mana wani abun kunyar a nan, na bar waccen unguwar saboda ke, nan dai kin ga mu baƙi ne babu wanda ya san tabonki ballantana ki rasa miji, ki nutsu don Allah kin ji?" Ta ce"In sha Allah Baaba ba zan ba ki kunya ba". 08028966015 [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS PAGE 3 Follow the AUTAR MANYA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h GIDAN HARUNA Halima ta tashi daga ƴar kwanciyar da ta yi a sallaya bayan idar da sallar isha'i, idonta fal bacci, saboda gajiyar da take kai wa dare da ita dalilin kujiba-kujibar da take wuni tana yi na sana'o'inta, ta yi murmushi tana yi wa mijinta sannu da zuwa, Haruna ya zauna yana amsawa, ya bata ledar hannunsa, da dubu ɗaya, ta karɓa tana yi masa godiya, sannan ta kawo masa abinci ta shige ɗaki ta kwanta, kafin ya gama har ta yi bacci. Ya ɗauki wayarsa ya kira Zainab suka yi fira, don ya san Halima tana da nauyin bacci ba za ta farka nan kusa ba. Can wajen ƙarfe goma har ya kwanta, Zainab ta kira shi ta ce ya kunna data, jansa ta dinga yi da maganganun banza, har ta tabbatar ta tada masa hankali sannan ta roƙe shi kan ya zo ya taya ta wanka, da farin ciki ya tashi tsam ya fice daga ɗakin, duk da yana fargaba, a tsakar gida suka yi kiciɓus suka yi wa juna murmushi ta cikin duhun, tana shiga banɗaki ya mara mata baya, ba su daɗe da shiga ba suka ji muryar Baaba tana cewa"Da mutum?" Lokaci ɗaya ƙirjinsu ya buga, suka fara muzurai, jin ana ƙoƙarin buɗe ƙyauren Zainab ta yi saurin cewa"Da mutum, ina ciki Baaba". A hankali ya ce"Yanzu ya za mu yi kenan?" Ta ce"Idan ta gaji za ta koma". Ya ce"Ta ya za ta koma tana buƙatar shiga banɗaki, kema wallahi kin fiya jaraba, ga shi za ki tona mana asiri". Ta ce"Tsautsayi ne, wallahi na gaji da marmarinka..." "Ni uwar me kike yi ne Zainab?" Baaba ta faɗa a fusace. Ta ce"Ina masai kuma yanzu na shiga". Suka ɗauki lokaci a haka kowa tsuru-tsuru musamman Haruna, sai Zainab ta tuna da ai da waya a hannunsa, da sauri ta ce"Ka kira lambata wayar tana ɗaki". Yana kira, ta ɗaga murya ta ce"Baaba ga wayata can tana ringing don Allah ki ɗaga kawo ne". Baaba da fitsari ya matse ta, a fusace ta ce"Ke buhun ubanki, wai kwana za ki yi a banɗakin?" Ta ce"Don Allah Baab, kuɗi ya ce zai turo, kin san kuma ba ya kira biyu, don Allah je ki kar ta katse kafin na fito". Baaba ta koma ɗaki tana tsaki, wuf Haruna ya fito ya yi zaure da sauri, sannan Zainab ɗin ta fito, ta tarar da Baaba tana kokowa da wayar, don ba ta iya ɗagawa ba, ta karɓi wayarta Baaba ta koma banɗaki tana mita, ita kuma ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya, sosai take son Haruna don haka dole ta san yadda za su ɓullowa lamarin nan, ta riga ta saba da maza yanzu jinta take tamkar a keje, don tun da suka dawo gidan nan ba ta haɗu da wani namijin ba, kuma a satin da za su dawo ɗin aka cire mata cikin da wani saurayinta ya yi mata, dalilin hakan ne ma kakar tata ta ce a bata Zainab ɗin su bar unguwar, saboda kowa ya ji zancen zubar da cikin nata, ta san idan Zainab ta ci gaba da zama a unguwar ba lallai ƴan ba ni na iya su barta ta yi aure ba. Shi kuwa Haruna sai da ya ji Baaba ta shiga banɗaki, sannan ya shiga ɗakinsa ya saka sakata, tashin Halima ya yi ya ragewa kansa zafi, saboda Zainab ta gama kunna shi, daga nan bacci mai cike da nutsuwa ya kwashe shi, saɓanin Zainab. GIDAN SADIQ Washegari da damuwa Yusra ta tashi, idan ta tuna maganarsu ta jiya sai gabanta ya faɗi, sosai ta shiga tsoron kar Sadiq ya ƙara aure, tana da kishi sosai, ba ta jin za ta iya raba mijinta da wata macen, a yadda take ji indai ta tabbata Sadiq zai ƙara aure ita za ta iya haƙura da aurensa bakiɗaya ma, ta je ta yi wani auren ta rayu ko da babu ƴaƴanta a kusa da ita, muddin za ta rayu babu kishiya kuma ba za a hana ta aikinta ba ta amince, a sanyaye take yin komai har ta kammala abun karyawa ta kai dining ta jera, sai da ta yi wanka sannan ta tashi yaran daga bacci, kasancewar yau Asabar ce babu makarantar boko, ta yi musu wanka, da suka ƙaraso dining ɗin shi Sadiq har ya gama cin nashi abincin ya tashi, yana kallonta ya san tana cikin damuwa, sai ya ɗauka ko yanayi ne jikin da jini, tun da ya tashi ba su haɗu ba sai yanzu, don tana idar da sallah kafin ya dawo daga masallaci ta koma ɗakin yaranta ta kwanta. "Zan fita, me za a kawo?" Ya tambaye ta yana yi mata kallon tsaf. Hankalinta a kan abincin da take zubawa ta ce"Ba sai ka aiko komai ba, yau ina gida me za a dafa maka?" Yana tafiya ya ce"Ki dafa zaɓinki kawai ya yi". Ya fita yana mamakin sauyinta, ko a dawo lafiya ba ta ce masa ba, ballantana ta raka shi, ya sauke ajiyar zuciya yana ƙoƙarin kau da abun. Da rana bayan ta gama komai yara sun tafi islamiyya, ta kwanta tana ta tunanin wannan maganar tasa da take neman tarwatsa mata farin ciki, idan ta tuna za su rabu sai idonta ya ciko da ƙwalla, kanta ya kulle ta rasa abun yi, saboda haka ta kira Sister Sumayya a waya, babbar ƙawarta tun ƙuruciya, kuma abokiyar aikinta a yanzu, ba sa ɓoyewa juna sirri damuwar ɗaya ta ɗayar ce, bayan sun gaisa Sumayya ta ce"Sister na ji kamar akwai damuwa a muryarki, ba ki da lafiya ko daga bacci kika tashi?" Yusra ta sauke ajiyar zuciya ta kwashe duk abin da yake damunta ta faɗa mata. Sumayya ta yi murmushi ta ce"Haba ƙawata, ke daga wannan kawai sai ki yi zargin Sadiq zai iya ƙara aure?" Yusra ta ce"Kamar ba ki san butulcin namiji ba?" "Butulci?" Sumayya ta tambaya da mamaki, sannan ta ɗora da faɗin"Don zai yi abin da Allah Ya halatta masa sai ki kira shi da butulu? Haba Yusra ki dawo cikin hayyacinki...". Ta katse ta da faɗin"Wallahi Sumayya ba zan zauna da kishiya ba, don haka zan ba shi zaɓi, ko ya sake ni ko ya manta da ana ƙara aure a duniya". Cike da mamaki Sumayya ta ce"Da gaske duk son da kike yi wa Sadiq za ki iya rabuwa da shi saboda zai ƙara aure?" Yusra ta ce"Ƙwarai kuwa, wannan abu ne mai sauƙi a wajena, saboda na tsani kishiya". Sumayya ta yi makirin murmushi mai ɗauke da manufofi da dama, wannan wata dama ce da ta jima tana neman hanyar samunta, domin kuwa ko maye ya manta uwar ɗiya ba za ta manta, amma za ta biyo mata ta bayan gida, kuma daki-daki har ta cim ma burinta. "Sister ya zan yi? Duk na damu". Yusra ta faɗa kamar za ta yi kuka. Sumayya ta ce"Dole cikin uku a yi ɗaya, ko dai ki haƙura da aikinki kamar yadda yake so, ko kuma ki samo ƴar aiki wacce za ta dinga zama tana yi miki aikin gida, idan kina aikin kwana ta kwana da yara ko kuma ki haƙura ya ƙara auren". Yusra ta yi shiru na sakanni tana nazari, sannan ta ce"Ba zan iya ajiye aikina ba fa, zan gwada yi masa zancen ƴar aikin dai ko zai amince". Sumayya ta ce"Idan ya amince sai ki yi min magana, zan samo miki mai hankali da nutsuwa, kin dai ƙi kishiyar ko? Ni ba ga shi ita ce take kula da ƴaƴan ba idan ba na nan?" Yusra ta taɓe baki ta ce"Zuciyarmu ba iri ɗaya ba ce Sister". Daga haka suka ɗan taɓa hira sannan suka yi sallama, da wannan matsayar ta samu sauƙin damuwar da take ji. Da daddare bayan sun gama cin abinci, yana lura da yanayinta na rashin sakewa da shi har yanzu, amma ya share, sai da ta gama jujjuya maganar tana tunanin karɓuwarta a wajensa sannan ta ce"Masoyi ina da magana mai muhimmanci". Ya ce"Ina sauraronki". Ta gyara zama ta kama hannunsa tana wasa da shi, ta ce"Na san ba na sauke duka nauyin da ya rataya a wuyana ta ɓangaren kula da gidan nan, ni ma ba na son zaman yara a maƙota, ga shi kai ma ana katse maka kasuwa, da safe a katse maka bacci ka tashi ka shirya su, su tafi makaanta..." "Ai duk na san wannan Yusra, ki tafi gaɓa ta gaba" Ya katse ta da faɗin hakan. Ta ce"Dama tunani na yi, na ce me zai hana na samo mana ƴar aiki, sai ta dinga kula da gidan idan ba na nan ko?" Ya yi shiru yana nazari, saboda bai taɓa zaton jin haka daga bakinta ba. "Ka amince na samo?" Ta tambaye shi jin ya yi shiru. Ya girgiza kai ya ce"Yusra ba na son ƴan aikin nan, kuma ma gidan nan bai yi girman da za a buƙaci ƴar aiki ba, indai don kula da yara ne, zan duba yiwuwar duk ranar da kike yin aikin kwana a kai su gidanmu su kwana a can, ni kuma zan kula da kaina, sai ki taya ni addu'ar Allah Ya ba ni ikon riƙe kaina, idan kuma na ga hakan duka bai yi daidai ba to ina ba ki haƙuri, don gaskiya zan iya ƙara aure..." "Wai da gaske?" Ta katse shi da tambaya, idanuwanta sun kawo ruwa, ya jinjina mata kai alamar tabbatarwa. Ta ce"Sadiq ka san zan iya haƙura da aurenka saboda kishiya?" Ya yi guntun murmushi ya ce"Ban sani ba, kamar yadda ke ma na tabbata ba ki san zan iya ƙara aure saboda na tsare mutuncina da tarbiyyar yarana ba ko?" Tashi ta yi za ta bar wurin, ya ruƙo hannunta, ta fizge hawaye suna sakko mata, ta shige ɗaki ta kwanta, tana kuka mai cin rai. ALI Bayan sallar isha'i yana shirye-shiryen komawa gida kwatsam sai ga Reza ta zo har majalisarsu, ya haɗe rai duk da yana ɗan fargaba saboda ya san ba ta da kirki, gefe ya ja ta don kar ta yi masa tonon silili a cikin mutane, ya ce"Haba Reza don Allah ki sakar min mara na yi fitsari!". Ta ce"Kai dalla can, ni harkar arziƙi ce na zo maka da ita, kana so na ka biya ni kuɗin?" Ya ce"Wallahi ina so, rashin kuɗin ne kawai, idan akwai ai ba zan bari ki yi ta bibiyata haka ba". Ta ce"To albishirinka". "Goro!" Ya faɗa cikin ƙosawa. Ta dafa kafaɗarsa ta ce"A daren nan za ka iya biyana cikin daɗin rai, wataƙil ma ka samu jari sanadin hakan". Ali ya ce"Don Allah Reza ta fi kai tsaye, sai kwana kike sha". Ta ce"Wallahi wata ƙawata ce take neman mai ɗauke mata kewa, ta kira ni ta ce na lalubo mata mai jini a jika, za ta ba shi dubu biyar, sai na ga tun da kana ta ƙoƙarin biyana awon shinkafa ya hana me zai hana ka je kawai, ka ga sai na riƙe kuɗin da za ta ba ka, ka biya ni kenan?" Ali ya ɗan sosa kai yana tunani, yana son zuwa yana fargabar kar ya daɗe ya shiga komar Maryam, amma wannan wata babbar dama ce, ko babu komai zai sauke duka kewar dake tattare da shi, sannan ya huta da nacin Reza na neman biyan bashinta, ya sauke numfashi ya ce"Ina ne gidan?" "Biyo ni!" Ta faɗa tana wucewa gaba, ya kai wa abokinsa Hamza mukullin babur ɗinsa yana faɗa masa yana zuwa,ya bi ta a baya zungui-zungui, suka shiga adaidaita sahu suka ɗauki hanya. Suna fara tafiya sai ga kiran Maryam ya shigo wayarsa, ya ƙi ɗauka don bai san me zai ce mata ba. A ƙofar wani babban gida suka tsaya, suka fito ta ɗauki waya ta yi kira, babu jimawa wata babbar mace ta fito ta ba wa Reza kuɗi idonta a kaina, sannan muka shiga Reza ta koma, sai ƙarewa gidan kallo nake, wanda nake mamakin a ce mace ce ita kaɗai take rayuwa a cikinsa, haka dai nake biye da ita har cikin babban falon da ya ji kayan more rayuwa, sanyin Ac sai ratsa ni yake yi, babu wani tsayawa bayani ta nemi gudanar da abin da ya kawo ni kai tsaye, ni kuwa ban yi ƙasa a gwiwa ba wurin faranta mata, har ban san tsawon lokacin da na ɗauka ba. Kafin na fito daga wanka ta kawo min abinci mai rai da lafiya, dama yunwa nake ji, na ci na ƙoshi na kora da lemo mai sanyi, sai a lokacin ta kalle ni ta ce"Ya sunanka?" "Aliyyu" Na ba ta amsa ina murmushi. Ita ma murmushin ta yi min ta ce"Gaskiya na ji daɗin haɗuwarmu, nawa Reza ta ba ka?" "Dubu biyar" Na ba ta amsa. Ta ce"Ni zan ƙara maka dubu biyar yanzu, sai dai babu cash a hannuna, kuma ATM ɗina ya samu matsala, ka kwanta ka huta bari na shiga maƙociyata ta ara mini, ko na daɗe kar ka fito". Ya jinjina mata kai cike da farin ciki, sai a lokacin ya duba wayarsa ya ga sha ɗaya saura mintuna, ga miss call ɗin Maryam rututu har da massages, tsoro ya kama shi, gabaɗaya hankalinsa ya tashi, Allah Ya taimake shi ba ta daɗe ba ta dawo, ta ba shi dubu biyar, sannan ta shiga kitchen ta fito da leda ta ba shi, ta ce"Ga mai adaidaita nan zai kai ka sauke ka, ka ga dare ya fara yi". Ya ce"Na gode sosai Hajiya". Suka yi musayar lamba, ya fita ya shiga adaidaita sahun yana yi masa kwatance har suka ƙarasa. A sanyaye ya ƙarasa gidan nashi, yana tura ya ji shi a rufe kamar yadda ya yi zato, ya ciro waya ya kira ta, bugu ɗaya ta ɗauka "Ki zo ki buɗe min, ina ƙofar gida". Ya faɗa da fargaba. Yana jin motsin buɗewarta, ya mayar da ledar hannunsa bayansa ya ɓoye, tana buɗewa ko kallonsa ba ta yi ba ta juya ta koma, ya rufe gidan ya ajiye ledar a zaure, ya shiga yana karanto la haula wa la ƙuwwata a hankali. 08028966015 [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS PAGE 4 Follow the AUTAR MANYA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN ALI Ɗakin gado ta shige kamar kububuwa, kafin ya ƙarasa har ta kwanta, ya ƙaraso ya zauna a sanyaye ya ce"Love ba ki san mene ne ya tsayar da ni ba..." Ta katse shi da faɗin"Babu ruwana da ko mene ne ya tsayar da kai, ka raba dare a waje, ni dai ba zan iya ba, don haka gobe ƙarfe shida a gidanmu za ta yi min in sha Allah!". "Innalillahi! Haba Maryamata, ai ya kamata ki ji hanzarina, wallahi aiki ne ya sha kaina, ganin ga azumi yana matsowa kuma ban tanadi komai ba, shi yasa na ce bari na dinga ƙara lokacin tashi saboda na linka samun kuɗin, amma tun da hakan bai yi miki ba, shi kenan na haƙura kawai". Ko juyowa ba ta yi ba, ballantana ta nuna ta san yana yi. Ya zaro dubu biyu yana miƙa mata ya ce"Ga wannan kya sayi hoda". 'Ko uwar hoda ba!' Ta faɗa a zuciyarta, tun da ba ta ga amfanin yin kwalliyarta ba, kafin ta yi wanka yake fita, sai dare ya dawo, da daddaren za ta yi ta zambaɗa hoda kamar wata aljana? Ta yi ƙwafa a bayyane. Ya tashi a sanyaye ya canza kaya, ya kashe wayarsa ya kwanta, sai kuma ya ba ta tausayi ganin bai ci abinci ba, bai yi wanka ba, duk da gajiya da yunwar da ya kwaso, kuma duka saboda ita yake yi, ya nemo mata abin da za ta ci ta sha da sutura, sai ta ji ba ta kyauta ba, to amma mazan zamanin nan ne sai kana saka ido sosai a kansu, idan ka ce za ka ɗaga musu ƙafa sai su fanɗare maka kana ji kana gani. "Baka yi wanka ba kuma abincinka yana falo" Ta faɗa ba tare da ta juyo ba. Ya ce"Babu komai, zan kwana a hakan". Ba ta sake cewa komai ba, ta tashi ta fita, ta ɗauki a bincin ta kai kitchen ta buɗe ta rufe da kwando saboda kar ya lalace, shi kuma yana ta fargabar kada tsautsayi ya sa ta leƙa zaure, wata fitinar ta ɓallo, sai da ta dawo ta kwanta sannan hankalinsa ya kwanta. Yana lura ta yi bacci ya tashi tsam, ya tafi zaure, ya ɗauki ajiyarsa ya buɗe, snacks ne da dangin kayan zaƙi su alawar madara da chocolate kala-kala, sai robar wani lafiyayyen yougurt, ya zauna a zauren ya buɗe yougurt yana sha, sannan ya kunna data yana duba sakwanni hankali kwance, ya kai minti talatin kafin ya tashi ya tattara sauran kayan, saɗaf-saɗaf ya shiga ɗaki, ya ɗakko wata babbar rigarsa ta shadda ya bazata ya jure su a ciki, ya ƙudundune ya cusa a sif, ya nemi waje ya kwanta bacci mai daɗi ya kwashe shi. Yana farkawa ya ga gari har ya yi haske, ya kalli agogo ya ga bakwai saura, ya tashi da sauri ya fito, falo ya leƙa ya tarar da Maryam zaune tana cin abinci ga kuma babban akwati a kusa da ita, gabansa ya faɗi, ya dai fita ya yi alwala ya dawo falon, a bakin ƙofa ya shimfiɗa salayya saboda kar ta fita yana sallah, yana idarwa ya ce"Maryam yanzu duk fushin ne ya sa kika ƙi tashina sallah har gari ya waye?" Ta ce"Ai dama ba dolena ba ne, kai ne yake dole ka tashe ni". Ya ce"To shi kuma wannan akwatin fa na mene ne?" Tana ajiye farantin hannunta ta ce"Gidanmu zan tafi Ali, don ba ƴar iska ka ajiye ba da har za ka kai ƙarfe goma sha ɗaya a waje! Gara na tafi idan ka gama tara kuɗin na dawo, idan kuma ka samu wata ma shi kenan". Ta ƙarasa maganar tana ɗaukar hijjabi za ta saka. Ya ƙarasa ya riƙe hijjabin kamar zai yi kuka ya ce"Haba don Allah Maryam, ai na san na yi kuskure tun da na ba ki haƙuri ya kamata ki yi min uzuri, ki gani ko zan ƙara? Naga jiya ne kawai hakan ta faru, kuma na faɗa miki dalilina, tun da ba mu fahimci juna ba na haƙura da aikin daren, wallahi haka ba zai sake faruwa ba, yi haƙuri mana kin ji kyakkyawar matata". Ta koma ta zauna tana ɓata rai ta ce"Wannan ya zama na ƙarshe, don idan ka ƙara kai wa irin haka a waje ba zan fahimce ka ba, wa ya faɗa maka zafin nema yana kawo samu?" Ali ya ce"Ba ma zai sake faruwa ba in sha Allah". "Ina ka bar babur ɗinka jiya?" Ta jefo masa tambaya. Ya ce"Ai da na ga na yi dare sai na bar shi a gidanmu saboda kar masu ƙwacen babur su tare ni". Sai da ya tabbatar ta haƙura sannan ya tafi wajen aiki, bayan la'asar sai ga wannan Hajiyar ta kira shi a waya, ya ɗaga suka gaisa take ce masa yau ma idan da dama tana son ganin shi, da sauri ya faɗa mata babu dama, suka yi sallama yana jin rashin jin daɗi, saboda yana son zuwan amma yana son zaman lafiya a gidansa don haka ya kau da kai, ya ci gaba da aikinsa. Sai bayan magriba Maryam ta ɗauki akwatinta ta mayar da kayan ta jere a sif, buɗe nashi sif ɗin tayi, don ta kwana biyu ba ta gyara ba, tana kwaso kayan ta ji motsin leda, da mamaki ta shiga bincikawa, ai kuwa tana zazzage babbar rigar nan sai ga kayan ciye-ciye sun bayyana, gabanta ya faɗi ta hau duba su cike da mamakin yaushe suka fara haka da Ali? Abun har ya kai ya sayi kayan daɗi ya ɓoye a sif yana ci shi kaɗai? Gefe ta yi da su, ta kwashi kayan ta mayar sif don ta fasa linkewar, ta kwashe kayan ƙwalam ɗin ta je ta baje a falo, ta dinga ci kamar babu komai, sai da ta cinye komai ta sha ruwa ta zubar da ledojin tana ta mamaki, tana kuma jiran dawowarsa don ta ji dalilin wannan sabon salon da ya tsiro da shi. Ƙarfe takwas tana yi Ali ya kamo hanyar gida, har kwakwa da dabino ya siya mata a hanya, saboda ya san tana so, ya tura ƙofar ya shiga da babur ɗinsa, ransa fes ya shiga ɗakin, ta kalle shi babu yabo babu fallasa ta yi masa sannu da zuwa, ya amsa yana miƙa mata ledar kwakwar, ta karɓa ta yi godiya tana jinjina rainin hankalinsa, wato ya siyo kayan ƙwala har da dambun nama, ita shi ne zai haɗa ta da kwakwa, ta maze ta kai masa ruwa ya yi wanka, ya fito ta zuba masa abinci ta koma kujera ta kame tana cin kwakwa da dabinon. Da ɗan mamaki ya kalle ta ya ce"Ya dai Love! Yau kin ci abinci kafin na dawo kenan". Ta girgiza kai ta ce"Wallahi ban ci ba". Ya ce"To me yasa?" Ta ce"A ƙoshe nake, nan da ka gan ni cikina babu masaka tsinke tura kwakwar nan kawai nake don ina so". Ya yi ƴar dariya ya ce"To ke kuwa me kika ci?" Ta ce"Abubuwan da ka ci jiya ka ƙoshi har ka kasa cin abincin dare". Gabansa ya faɗi ya dake ya ce"Kamar ya? Me na ci jiyan?" Maryam ta ce"Au har ka manta ka yi saura ka ajiye a sif kenan". Ya ji ƙirjinsa ya ba da sautin dumm! Ya kasa cewa komai. Ta ce"Hmm! Na yi mamaki wallahi, yaushe muka fara haka da kai? Kuma idan za ka ci kai kaɗai ai da sai ka ci abunka a waje, ban gani ba ballantana na saka maka rani..." Ya katse ta da faɗin"Wallahi ba haka ba ne Maryam, wata yarinya ce take ta bi na a kwanakin nan ba na kula ta, to shi ne jiya ta bawa Hamza ya kawo min wannan kayan, kuma na san idan ma ban karɓa ba wallahi ba zai mayar ba, kuma zuwa zai yi ya ce mata na karɓa, shi yasa kawai na karɓa ɗin, to da yake na san ba za ki ji daɗi ba shi ne na ɓoye saboda kar ki gani, amma ba wai manufata na yi miki rowa ba wallahi". Maryam ta yi murmushin takaici ta ce"To mene ne abun ɓoyewa? Kenan jiyan a wurinta kake har sha ɗaya ko?" Ya yi saurin girgiza kai ya ce"Wallahi ban taɓa kula ta ba ma, ba faɗa miki ai aiki na tsaya, kuma tun da zai kawo mana matsala na daina, ba ga shi yau na dawo da wuri ba?" Ta ce"To shi kenan magana ta wuce". GIDAN SADIQ Sanda Sadiq ya gama uzurinsa ya je zai kwanta, sai ya same ta zaune a kan gadon, yana shiga ta sakko ta fice daga ɗakin, har bacci ya fara fizgarsa ba ta shigo ba, hakan ya sa ya fito don ya lallashe ta, a falo ya tarar da ita kamar yadda ya yi zato, saboda halinta idan suka yi faɗa ta ce za ta kwana a falo, zama ya yi a gefen kujerar da take kwance, yana shafa kanta ya ce"Yusra!". Ta juya masa baya, ya juyo da ita ya ce"Ni fa ban ce miki zan yi wani auren nan kusa ba". Ta ce"To me yasa ka hana ni samo ƴar aikin?" "To ki samo mai hankali" Ta ji furucinsa a bazata. "Da gaske?" Ta tambaye shi tana jin daɗi sosai. Ya ce"Da gaske mana, ba shi ne dalilin fushin ba?" A gabansa ta ɗauki waya ta kira Sumayya ta faɗa mata ya amince da ɗaukar ƴar aikin, cikin jin daɗi ta ce mata gobe za ta kawo mata ita har gida. Sai ga Yusra ta ware har tana yi masa firar yadda za ta kasance da ƴar aikin, suka kwanta tana cike da farin ciki. Washegari da kuzarinta ta gama komai na gidan, shi kuma ya tafi shago, ƙarfe tara Sumayya ta shigo gidan tare da wata buduruwa, Yusra ta tare su da murna, suka gaisa tana kallon yarinyar da take a nutse daga gani ba ta da hayaniya, Sumayya ta ce"To ga Kursum nan na kawo miki, ban fiya yabon wani ba, amma ina da tabbacin za ki ji daɗin zama da ita, ba ta da gandar aiki, kuma tana da hankali". Yusra ta ce"Ai na lura da hakan, ke dai Allah Ya saka ƙawata". Sumayya ta ce"To ya kika tsara yanayin aikin, a nan za ta zauna duka ko zuwa za ta dinga yi tana tafiya?" Yusra ta ce"Idan ta gama aikinta za ta jira na dawo gidan sannan na tafi, ranar da nake aikin kwana kuma za ta kwana a nan, ta kula da yaran ko dan saboda tashin sassafe ta shirya su su tafi makaranta". Nan Sumayya ta faɗa mata unguwar da gidan su Kursum yake, sannan ta ɗora da faɗin"Kursum ki yi abin da ya kawo ki shi kaɗai, ki kular mata da yaranta ki rungume su hannu biyu-biyu, sannan idan za ki yi girki ban da almubazzaranci, magana ta ƙarshe babu ruwanki da mijinta! Gaisuwa ce kaɗai za ta haɗa ku, idan kin yi girki ki ajiye a dining, yana dawowa ki shige ɗakin yara a nan za ki na kwana, kar ki sake ki fito babu hijjabi ko mayafi idan yana gida, kin dai ji ko!?" Ta ƙarasa tana ƙanƙance ido alamar gargaɗi sosai. Kursum ta ce"In sha Allah zan kiyaye komai". Yusra cikin jin daɗi ta ce"Na gode sosai ƙawata". Sannan ta ce"Yau babu aikin komai, tun da ina gida, sai dai gobe ki zo da safe, zan bar miki mukulli a wurin mijina, sai ki dinga zuwa kina karɓa a shagon, kin ga gobe aikin safe zan yi, to kafin ki zo mun fita dukanmu, idan kin karɓo mukulli sai ki yi wanke-wanke ki gyara ko'ina, kafin sha biyu ki yi girki idan yara sun dawo su ci ki shirya su su tafi islamiyya, shi ma ki zuba ki kai masa nasa, sai ki zauna a gidan, wajan ƙarfe uku zan dawo kin ga sai ki tafi ko?" Kursum ta jinjina kai ta ce"In sha Allah babu matsala". Suka yi mata sallama suka tafi, a hanya Sumayya ta ce"Don Allah Kursum kar ki ba ni kunya, na faɗa miki kuɗin da zan biya ki idan aikin nan ya yi kyau, ki kwantar mata da kai, shi kuma ki san ta inda za ki ɓullo masa". Kursum ta yi murmushi ta ce"Ni fa dama can yana burge ni wallahi, ballantana kuma za mu rayu a inuwa ɗaya? Hmm Allah Ya kai damo ga harawa, ko bai ci ba ya yi ɓarna". Sumayya ta ce"Allah Ya shi miki albarka Kursum, idan komai ya tafi daidai, wallahi sai na yi wata shida muna raba daidan albashina da ke". Kursum ta kwashe da dariya cike da farin ciki, ta ce"Riba biyu inji sauro". 08028966015 [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS PAGE 5 Follow the AUTAR MANYA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN HARUNA A ranar tun tsakar dare zazzaɓi ya rufe Halima, dama tun da rana take ciwon kai, ta kasa bacci, sai gabannin asuba ya ɗauke ta, amma da alarm ɗinta ya buga haka ta daure ta tashi ta yi sallah, sai dai ta kasa komai ta kwanta a sallayar tana ta rawar sanyi, yayinda Haruna yake ta baccinsa bai san halin da take ciki ba. Zainab ganin har bakwai ta wuce Halima ba ta fito ba, ya sa ta ƙarasa ƙofar ɗakinta tana sallama, ta amsa mata da ƙyar tana tashi zaune ta ce"Zainab". Zainab ta buɗe labulen, ta ce"Halima yau lafiya kuwa ba ki fito ba?" Halima ta ce"Wallahi ba ni da lafiya, zazzaɓi da ciwon kai tun jiya, yau ba zan iya ba ma". Zainab ta ce"Ai kuwa babu daɗi a zo nema a ga ba ki yi ba, yau ɗaya da sai na yi miki". Halima ta ce"Za ki iya kuwa Zainab? Kar ki wahalar da kanki". Ta ce"Haba wace wahala, ɗakko min kayan, bari na haɗa wuta". Ta fita tana kunna mangal, ita kuma Halima ta tashi ta ɗakko mata kayan wainar, Zainab ta dawo hannunta ɗauke da kofin kunu ta miƙa mata, har da paracitamol ta ce ta sha kafin a kaita asibiti, ta yi mata godiya, ita kuma ta koma ta fara aikinta. Wajan ƙarfe tara Haruna ya tashi daga bacci, turus ya yi ganinta kwance a daidai wannan lokacin, ya fice don shiga banɗaki, sai dai ya tsaya ganin Zainab a bakin murhu tana ta fifita wutar wake da shinkafa, don har an fita da waina, jikinta ne ya ba ta ana kallonta, ta ɗago ta kalle shi, ta yi masa farr da ido, ƙasa-ƙasa ya ce"Ke dai kina son wahalar da kanki, ki yi ta taya matar nan aiki". A hankali ta ƙaraso kusa da shi ta ce"Kai ka tattarata ka kai ta gida ta yi jinya, ka ga mun samu ɗaki kafin ta dawo". Zai yi magana kenan Baaba ta fito daga ɗaki don ta duba jikin Halima, suka waske ya wuce banɗaki, a ransa yana ta tunanin maganar Zainab, domin tabbas shawararta abar dubawa ce, saboda haka yana komawa ɗaki ya tambayi Halima kwanciyar me take yi, ta faɗa masa yanayin jikinta, ya ce"Allah Ya sawaƙe, to ina abun karyawata?" Ta ce"Ban fita ba fa yau kwata-kwata". Ya ce"Kuma don ba ki da lafiya ba zan ci abinci ba kenan?" Takaici ya kamata, tana tabbatarwa kanta lallai Haruna ba miji ba ne, ba ta gama tsinkewa ba sai da ta ji muryarsa ya ce"Daurewa fa za ki yi ki dafa min taliyar nan". "To!" Ta amsa tana tashi zaune, ta huta na sakanni sannan ta fita ta kunna mangal ta ɗora. Tana fita ya kira lambar Zainab, tana ɗagawa ya ce"Na koro ta ta min girki, kar ki taya ta, ni abincin ma ban so kika karɓar mata ba, idan ta ji wahala za ta nemi zuwa gidan da kanta". Zainab ta yi dariya suka kashe wayar, tana leƙen Halima ta gefen labule. Zama ta yi a bakin wutar bayan ta haɗa komai na jollop ta ɗora, ruwan yana tafasa ƙamshin ya daki hancinta, nan take cikinta ya fara rugugi, yawu ya taru a bakinta da gudu ta ƙarasa bakin makwarara ta fara kwara amai babu ƙaƙƙautawa, Zainab ta yi kamar ba ta ji ta ba, haka shi ma Haruna, sai Baaba ce da ta ji abun ya ƙi ƙarewa ta fita tana cewa"Subhallah! Sannu Halima, har da amai?" Halima ta gyaɗa kai a galabaice, Baaba ta miƙa mata buta ta wanke bakinta, ta wanke wurin tana ta yi mata sannu, Halima ta koma ta zauna a wurin girkin, tana buɗewa don ta zubar taliyar wani aman ya sake taso mata, haka ta dinga yi babu ƙaƙƙautawa, wannan karon Baaba cewa ta yi"Zainab je ki ki ƙarasa mata girkin can, ina ga ƙamshin ne yake saka ta aman nan". Zainab ta je kan girkin, Baaba ta yi sallama a ɗakin Zainab tana kiran Haruna, ya fito yana gaishe ta, ta ce"Haruna wannan yarinyar kamata ya yi fa ku tafi asibiti, ka ga duk ƙarfin halinta ta galabaita lokaci ɗaya". Ya ce"To Baaba bari ta shirya sai na kai ta". Ɗaki ta koma ta kwanta, ya kalle ta yana taɓe baki ya yi mata sannu, ta gyaɗa masa kai, Zainab tana gama girkin ta yi sallama a ɗakin, ta ɗauki kula a kwando ta juyo taliyar ta kawo musu, suka faki idon Halima suka kashewa juna ido. Yana cikin cin taliyar yake cewa"Halima asibiti ya kamata na kai ki, ga shi da ɗari biyar kawai na tashi, kin ga kuwa ba ta fi kuɗin adaidaita ba, yanzu ya za a yi?" Ta ce"Babu komai, ai na sha paracitamol". Ya ce"To me zai yi miki? Ba ki ga har da amai ba? Ko ciki ne da ke ma?" Cikin ƙosawa ta ce"Allah masani". Ya ce"To yanzu dai tashi za ki yi, ki lallaɓa ki shirya, ki saka kayanki ko kala uku ne a jaka sai na raka ki gidanku, idan jikin ya yi dama-dama kya dawo". Cikin rashin son hakan ta ce"Gaskiya da ka bar ni a nan ɗin..." "A hakan ba kya iya aikin komai? Daga dafa taliya kin yi amai sau biyu, ina za ki iya wani moruwa? Duk aikace-aikacen gidan waye zai na yi miki?" Hawaye ya zubo mata, ta san gaskiya ya faɗa mata, saboda haka ta ce"To shi kenan mu tafi ɗin". Tana jiri ta ɗakko ƙaramin akwatinta, ta zuba kaya, ta saka hijjabi ta kwanta a kujera tana jiransa, yana gamawa ya ce ta tashi su tafi, sanda suka fito Zainab tana daka yaji, Baaba tana zaune a tsakar gida, Halima ta ƙirƙiri murmushi ta ce"Baaba za mu tafi". Baaba ta ce"Asibitin ne? Ya na ga akwati?" Haruna ya ce"Ai daga can gida zan kai ta, kin ga yanayin jikinta a gidan sai ta fi hutawa". Baaba ta ce"Haba ɗan nan! Irin haka ai babu daɗi yarinya tana fara laulayi ka kwashe ta ka kai gida, ban da abunka ba ga Zainab ba? Komai za ta yi mata, ga ni kuma zan dinga kula da ita, idan zazzaɓin ya sauka ai shikenan ma, ka dai duba". Ya ce"Ai Baaba wannan duk wahalar da ku za a yi, ita ma ta fi son zuwa gidan, ko kwana biyu ne ta yi sai ta dawo, kin san halinta idan tana nan ba za ta huta ba". Baaba ta ce"Ai shi kenan, kuma abincin da Halima?" Halima ta ce"Zainab ta dinga yi, sai ta dinga cire ribarta ta ajiye min uwar kuɗin, har mu ga yanayin jikin". Ta yi mata godiya, Zainab ta raka su har ƙofar gida, tana farin ciki. A ƙofar gidansu ya tsaya ko shiga bai yi ba ya ba ta ɗari biyu ya juya ya tafi, ta shiga da sallama tana jin jiri kamar za ta faɗi, nan ta faɗawa mahaifiyarta halin da ake ciki, Umma ta taɓe baki ta ce"Ke kuma ta ki ƙaddarar kenan Halima, wannan mijin naki sam ba mutum ba ne wallahi, amma babu komai lokaci ne". Ta haɗa mata shayi ta sha da biredi, ta dafa mata ruwa ta yi wanka, ta fita ta siyo mata magunguna ta sha, ta kwanta bacci ya ɗauke ta. Haka Zainab ta gama abinci ta siyar ta ware ribarta, ta yo cefanen wanda za ta yi gobe. Tun kafin dare sun tsara yadda komai zai kasance, saboda haka dukansu babu wanda ya iya yin bacci, ƙarfe ɗaya na dare Baaba ta yi nisa a bacci, Zainab ta tashi ta zare sakata a hankali, ta fito ta tura ɗakin Halima da yake a buɗe babu sakata, dama yana zaune a falo yana jiranta, ya tashi da farinciki ya saka sakata, ya ja ta suka shiga uwar ɗaka, har kan gadon Halima. GIDAN ALI Washegari ƙalau suka tashi da Maryam komai ya wuce, ya ci abinci ya tafi aiki, wajan la'asar Hajiya ta kira shi, take tambayarsa yau zai samu lokacinta? Ali ya ce"Wallahi Hajiya ina wajen aiki ne..." Hajiya ta ce"Haba Aliyyu aikinka ai babu abin da zai tsare maka, idan ka tashi ba sai ka zo ba? Na ji daɗin haɗuwa da kai ne fa, shi yasa ka ga har ina nemanka, dubu goma zan baka wannan karon". Ali ya yi jimm yana jinjina dubu goma, da dubu goman nan fa zai rage aiki, don haka gaskiya ba zai bar wannan damar ta wuce shi ba, ya ce"To zan zo idan an yi sallar magriba, sai dai gaskiya ba zan daɗe ba". Ta yi murmushin jin daɗi ta ce"Babu damuwa, Allah Ya kawo ka lafiya". Yana aiki yana tunani, ga Baby Farha ma ta takura masa sai ya je gidansu, sai kaucewa yake don so yake ya yi sabon ɗinki, idan kuwa yana so da wuri dole ya jajje wurin Hajiyar nan idan ya tattara ya gama buƙatunsa ya watsar da ita daga baya, ana idar da sallar magriba ko gidansu bai shiga ba, ya buga babur ɗinsa ya tafi. A ƙofa ya tsaya ya faɗa mata ya zo, ta fito ta shiga da shi har babur ɗinsa, cike da farin ciki ta buɗe firji ta ba shi lemo me sanyi ya sha, sannan ya ce mata zai yi wanka, ta ce ita ma za ta yi dama, ba dan ya so ba suka yi wankan tare, ta kawo masa kayan ƙwalam yana ci tana kallonsa, sosai yaron ya shiga ranta, ta ce"Aliyyu kana burge ni sosai, kuma ina hango faruwar wasu muhimman lamura a tarayyarmu da kai, ga ka matashi mai jini a jika, a ina kuka haɗu da Reza?" Ya sosa kai ya ce"Hajiya kenan, Reza a ƙasan layinmu take, mun daɗe da ita". Ta ce"Waye kai? Ka ba ni labarinka, me yasa ka zaɓi neman mata a maimakon aure?" Ya ce"Hajiya ai ina da auren, wannan ana yin sa ne saboda nishaɗi kawai". Da mamaki ta ce"Da gaske kai ma kana da auren?" Ya ce"Wallahi ina da mata, yanayi ne kawai ya sa ban daina harkar nan ba". Ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Ni ma ina da miji..." Ya zaro ido da mamaki ya ce"Yanzu haka maganar nan da muke yi da auren wani a kanki?" Ta ce"Ƙwarai kuwa, amma ga ni nan ina dai amsa sunan matar aure ne kawai". Ya ce"Amma Hajiya me yasa kika zaɓi wannan rayuwar?" Ta yi murmushin takaici ta ce"Aliyyu Wani Auren ba ya amfanar mutum da komai sai cutarwa, wani auren na jeka-na-yi-ka ne, wani auren sai dai ya kai mutum ga halaka, wani auren ana yinsa ne saboda mugunta da ƙuntatawa, wani auren ana yinsa ne saboda asiri ya rufu, kamar dai nawa auren, ina zaune a gidan nan ne kawai saboda asirina ya rufu, tun ina yarinya a haka rayuwar take, an aura min wanda ba sa'an aurena ba, ya rufe ni a gida saboda mugunta yana can yana yawon ƙasashe da sunan aiki, ko yana nan babu abin da yake iya taɓukawa, girma ya kama shi duk ya gajiya, kuma a hakan mu uku ne matansa, cikinmu babu wacce ta taɓa ko ɓatan wata, rashin haihuwa daga shi ne, ga shi zan tsufa babu ɗa ballantana jika, gani yake tun da ya bar min dukiya ya sallame ni, ya manta ni mai lafiya ce ba kamar shi ba, ina buƙatar abokin rayuwa, shiyasa nake amfani da kuɗin da yake taƙama da shi ina yin abin da ya kasa yi min, Aliyyu ka ga laifina?" Har zuciyarsa ya san ba a kan daidai take ba, hujjarta ta yi rauni, tun da ai akwai hukuma, za ta iya kai shi a raba auren tun kafin abun ya yi nisa, amma dayake ya san ba wa'azi ya zo yi ba, sai ya ce"Gaskiya Hajiya ban ga laifinki ba wallahi, ai wannan shi ne daidai, mace sai da namiji, tun da har ya bar kuɗin ki ji daɗinki kawai, sai ki ta istigfari Allah gafurur rahim ne". Ta yi murmushin jin daɗi ta ce"Na gode sosai Aliyyu". Sun ɗauki tsawon lokaci suna aikata masha'a, shi kansa ya yi mamaki, saboda ya manta rabon da ya yi irin wannan daɗewar da mace, yau kam wasai ya ji shi kamar ya gama juye duk wata damuwarsa ta wannan ɓangaren, wani abu da bai sani ba Hajiya ta faki idonsa ta kashe wayarsa, Maryam har ta gaji da kira tana ji a kashe, sam ƙin ba shi damar tashi Hajiya ta yi, shi ma ya gaji sosai, don haka da taimakon sanyin AC bacci ya yi awon gaba da shi, ba shi ya farka ba sai ƙarfe biyu na dare. A firgice ya tashi zaune tunowa da inda yake, ƙirjinsa ya buga da ƙarfi lokacin da ya kalli agogo, ya ɗauki wayarsa yana mamakin yadda aka yi ta mutu, ya kunna gabansa yana faɗuwa, ya sakko daga gadon, ya zura kayansa sannan ya tashi Hajiya. Ta tashi tana mirtsika ido ta ce"Aliyyu ina zuwa? Ka kwana a nan don Allah". Da sauri ya ce"Ina? Ba zai yiwu ba wallahi". Ta tashi zaune tana narkewa kamar yarinya ta ce"Don Allah ka kwana, zan ƙara maka dubu goma". Ya ce"Ba ki san masifar da take tunkaro ni ba ne, wallahi ko a dubu ɗari ba zan kwana a nan ba". Ta tashi ta ɗakko masa dubu ashirin ta ba shi, ta ce"Amma ka san ba za ka keta unguwar nan a babur ba cikin daren nan". Ya ce"Wallahi zan tafi ko a ƙafa ne, iya wuya dai a gidana zan kwana". Hajiya ta ce"Ina zuwa" Ta ɗauki wayarta ta kira wata lamba, ta faɗa masa ya zo gidanta yanzu da sauri, tana sauke wayar ya ce"Waye?" "Ɗan sanda ne". Ta faɗa tana ajiye wayar ta zauna tana dafe kai, don ta tsani a katse mata bacci. Ba ta lura da daskarewar da Aliyyu ya yi ba, sai da ta ji cikin tashin hankali ya ce"Ɗan sanda fa kika ce! Hajiya me na yi miki?" Ta kalle shi ta kwashe da dariya ta ce"Aliyyu kenan!" ANA TA TAMBAYATA WAI WANI AUREN NA KUƊI NE? E NA KUƊI NE, A KAN NAIRA 300 KACAL! 08028966015 [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS PAGE 6 https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 ALI Sosai ya shiga tashin hankali, kamar zai yi kuka ya ce"Hajiya me na yi miki don Allah za ki saka mini da wannan?" Ta yi dariya ta ce"Ni kuwa ko butulu ce ai ba zan saka maka da sharri ba a yau, ko don faranta min da ka yi, haka kake da tsoro? Idan ka fita yanzu za a iya kama ka da laifin yawon dare, shi yasa zan saka Ɗan sanda ya mayar da kai har gida". Ya sauke ajiyar zuciya duk da haka bai samu nutsuwa ba, Hajiya ta ce"A gaskiya Aliyyu wannan matar taka ta yi dace, ina ma ina da damar yin wani auren! Ai da kai zan aura, don Allah gobe ma ka zo ka ji?" Ya ce"Hajiya kenan, ki bar ni na fara fita daga bala'in da na shiga yau, kafin komai ya biyo baya". Ta ce"Bala'i kamar ya?" Ya ce"Daga baya zan ba ki kabarin wace ce matata". Suka yi shiru, har Ɗan sandan ya kira ta ya ce ya ƙaraso, suka fita tare Ali ya hau bayan babur ɗinsa ya kai shi har ƙofar gida, ƙirjinsa yana ta bugawa ya ɗakko waya ya kira lambar Maryam yana haɗawa da ƙwanƙwasa gidan. Maryam da ba ta daɗe da yin bacci ba ta tashi a firgice jin ƙarar wayarta, tana dubawa ta ga shi ne, ƙwanƙwasa gidan da ake yi ne ya tabbatar mata da dawowarsa, ta duba lokaci ta ga ƙarfe biyu da mintuna, ta yi huci mai zafi zuciyarta tana ƙuna, ta sakko ta buɗe loka ta ɗakko mukullin shago ta shiga falo ta ɗakko tabarma tana buɗe gidan ta watsa masa ta mayar da sakata. "Maryam!" Ya kira sunanta yana buga ƙofar, amma ko waige ba ta yi ba, ta koma ɗakinta, zama ta yi a kan gadon tana tunanin wace rayuwa mijinta yake son faɗawa? Zargi ne kala-kala yake ɗarsuwa a ranta, ciki har da na neman matan, amma ta saka a ranta ko ma mene ne ya zo ƙarshe daga yau, ta share hawayen da ya zubo mata, duk yadda yake buga gidan ba ta sake bi ta kansa ba, ta kwanta da baƙinciki tare da fargabar sabuwar rayuwar da ya ɗakko. Shi kuwa Ali sosai ransa ya ɓaci, don tun da take cewa za ta ba shi tabarma ya kwana a waje bai taɓa zaton za ta iya aikatawa ba, sai ga shi ya ga zahiri, haskawa ya yi ya ɗauki mukullin ya buɗe ƙaramin shagon dake manne da gidan, ya shiga da bisimillah, duk ya yi ƙura don ba a taɓa kwana a cikinsa ba ma, haka ya shimfiɗa tabarma ya zauna, ya yi jugum yana nadamar wannan rayuwar da yake yi, ga shi aurensu ko shekara bai yi ba za su fara samun matsala, ya san gobe Allah ne kaɗai ya san irin bidirin da za su sha da Maryam, sai dai duk rintse ba zai yarda ta tafi gida ba, idan ta je ta faɗi dalili a ka titsiye shi da tambayar inda ya je me zai ce? Da wannan tunanin ya kwanta ya yi matashi da hannunsa, sai dai ya kasa bacci duk da babu sauro, tunani yake yi yanzu ya baro lafiyayyiyar katifa a makeke gado cikin AC, cikin abin da bai fi minti talatin ba rayuwarsa ta canza ga shi kwance a tabarma cikin ɗaki mai ƙura. Tashi zaune ya yi, ya lumshe ido yana tuna duk abubuwan da suka wakana a daren na yau, tsakaninsa da Hajiyar da ko sunanta ba ta faɗa masa ba, yana buƙatar kuɗi kuma ya ga alamar zai samu alkhairi sosai ta wajanta, muddin ya kwantar da kai, saboda haka dole a yi ɗaya cikin biyu, ko dai ya nunawa Maryam dole ta yarda da cewar ya samu sabon aikin dare na gadi a wani kamfani ko kuma ita Hajiyar ta yarda ya dinga zuwar mata da rana, sai ya dinga tashi daga aikinsa da wuri, idan ya tara abin da yake nema sai ya rabu da ita, da wannan tunanin zuciyarsa ta nutsu, ya ɗakko waya ya kira ta don ya sake yi mata godiyar kuɗin, sai dai ba ta ɗauka ba, ya kunna data yana duba saƙonni, sai wajen uku da rabi ya yi bacci. Da safe ƙarfe shida ya farka, ya fito ya ci gaba da buga gidan, ta ƙi buɗewa, ya kira wayarta sai ta ɗauka, ya ce"Maryam ki buɗe min alwala zan yi". Ta ƙashe wayar, ta zo ta buɗe, ya shigo a sanyaye ta kalle shi ta kau da kai, ya yi alwala ya yi sallah, yana zaune a falo ya ga ta ɗora tukunya, sannan ta koma ɗakin gado, ya tashi ya bi ta, yana shiga ya ga tana birkito kayan cikin sif tana watso su kan gado, ya ƙarasa ya tsaya a gabanta ya ce"Maryam mene ne haka? Wai me yasa kike sha'awar yin yaji ne? Ko ba ki san abun kunya ba ne? Yanzu ko cewa na yi ki tafi gida sai ki tafi ɗin? Sai ka ce kin manta da muna da magauta masu jiran su ga ranar da za ki yi nadamar aurena? Haba Maryam, komai fa nake yi dominki ne, na san tun farko na yi kuskure da na ɓoye miki abin da ya kamata a ce kin sani". Ganin ta ba da ni nutsuwarta, ya sa na zaunar da ita, ni ma na zauna na ci gaba"Maryam tsakani da Allah wani aiki ne na samu, na gadi da za mu dinga yi ni da a Hamza a wani kamfani, mu ne masu night duty, to shi ne dalilin kai wa daren da na yi jiya, ba a tashi ba ma na gudo saboda na san ba za ki samu nutsuwa ba, tun da ba ki san inda nake ba". Har yanzu ba ta ce komai ba. Ya ce"Gani na yi kuɗin da za su dinga biya da kauri shi yasa, kin ga fa kullum dubu uku, kin ga ai za mu toshe wani wajen ko?" Sosai ta yarda da shi, amma ba ta jin za ta yarda da wannan aikin daren, ta kalle shi ta ce"Yanzu saboda dubu uku za ka dinga kwana a waje kullum? Da rana kuma ka tafi wani aikin? Shi kenan ba ka da lokacin hutu? Shi baccin da wane lokaci za ka dinga yi? Tara shi za ka yi ya zame maka matsalar da sai ka sha maganin da ya ninka dubu uku sau goma? Ina ta faɗa maka zafin nema ba ya kawo samu, saboda haka ka kwantar da hankalinka, indai ni ce kar ka damu, ba ga shi ina sana'ata ba? Idan nauyin gidan ne ya maka yawa zama ya kamata mu yi mu tsara komai na san ta inda zan rage maka nauyi, ko magi da kayan miya ne, ba wai ka ɗauki wannan matakin ba". Ya ji daɗin yadda ta yarda da shi sosai, ya ce"Na gode Allah da ya ba ni mace ta gari, Maryam Allah Ya biya ki da gidan aljanna, yanzu dai aikin ne ba kya so ko?" Ta ce"E gaskiya ban yarda da shi ba". Ya ce"Dama shi komai ɗan maslaha ne, in sha Allah na haƙura, sannan Maryam ni ban amince ki taimake ni da abin da yake nauyina ba, zan dinga yi miki komai daidai ƙarfina, fatana dai mu samu zaman lafiya da farinciki mai ɗorewa". Tana murmushi ta ce"Allah Ya dawwamar mana". Ya ce"Yanzu dai tun da komai ya wuce shi kenan babu sauran rigima ko?" Ta ce"Da saura fa". Ya ce"To me kuma ya faru?" Ta ce"A gaskiya wannan majalisar taku ba na sonta kwata-kwata, kawai ana idar da sallar magriba ka dawo gida mu zauna ina buƙatar ganinka, mu yi fira na yi maka kwalliya kuma ka samu isasshen bacci". Ya yi dariya ya ce"An gama ranki ya daɗe, in sha Allah yau ana magriba za ki gan ni". Daga haka ta fita ta sauke shayinta, suka karya ransu fes, ya fita aiki cikin kwanciyar hankali. GIDAN SADIQ Da Sadiq ya dawo ta yi masa bayanin duk yadda komai zai kasance da ƴar aikinsu, ya amince ba don ransa yana so ba, sai dai a zauna lafiya kawai. Washegari da safe Yusra ta tafi aiki, don ta riga yaran fita a gida ta bar su da Sadiq, wajan ƙarfe takwas yana shago sai ga yarinya ta shigo, ta gaishe shi, ya yi zaton ma wani abu za ta siya, ganin ta yi shiru tana sunkuyar da kai ya ce"Me kike so?" Ta ce"Mukulli na zo karɓa, ni ce Kursum, sabuwar mai aikinku". "Ok" Ya faɗa yana kallon yanayinta, sannan ya ɗakko ya ba ta, ta duƙa ta karɓa ta ce"Na gode, sai anjima". Ta fice. Tana shiga gidan ta cire hijjabi ta yi gefe da shi, tana ƙarewa ko'ina kallo, mukullan ta fara gwadawa tana buɗe ɗakunan, sai ta lura babu na bedroom ɗin Yusra, ta taɓe baki ta shiga kitchen ta yi wanke-wanke, ta fito ta share ko'ina ta goge, ta share tsakar gidan har da wanke kayan su Afna duka, sannan ta ɗora girki, a cikin jakarta ta fito da leda mai ɗauke da magi, curry kala biyu da niƙaƙƙen nama soyayye, ta tsara haɗalliyar jollop, sannan ta kunna ɗayan gas ɗin ta ɗora wani girkin, ta saka magi da curryn da ta tarar a gidan, kafin ya dahu ta yi wanka ta ci kwalliyarya ta canza kaya, don da wasu kayan ta taho, tana gamawa ta zuba ta ci ta ƙoshi, ta juye ɗayar tukunyar wacce ta dafa kaɗan don Yusra, ta zuba na Sadiq ta rufe gidan ta tafi kai masa, a lokacin sha biyu saura kwata, tana zuwa ta ga ƙofar shagon a rufe, ta jira har shiru bai dawo ba, ganin har sha biyu ta yi ya sa ta koma gida saboda kar yaran su dawo, babu jimawa kuwa suka dawo, da saurinta ta tare su ta rungume su, suka tsaya suna kallon juna, duk da Momynsu ta faɗa musu ita za su dinga tararwa a gidan, kuma sun ganta ranar da ta zo. Hannunsu ta ja suka ƙarasa ɗaki, tana cewa "Sannunku ƙawayena kun gaji ko?" Suka gyaɗa mata kai. Ta cire musu unifom, ta yi musu wanka suna ta bin ta da ido, ta saka musu kaya marasa nauyi, sannan ta zubo musu abinci a faranti ɗaya, ta zauna tana ba su a baki tana yi musu murmushi har suka ƙoshi, sun ci sosai, saboda canjin test ɗin abinci da suka samu, ba irin wanda Yusra ta saba dafawa ba, ta ba su ruwa suka sha, sannan ta ɗakko jakarsu ta taya su home work, suna gamawa ta saka musu unifom ɗin islamiyya ta ɗakko alawowi ta ba su, ta zauna tana musu tatsuniya, har lokacin makaranta ya yi, da yake babu nida da yaran maƙota suke tafiya, ta ce daga yau ita za ta dinga raka su, sai da ta sake gyara fuskarta sannan ta ɗauki abincin babansu suka tafi, ta kai su makarantar ta ƙarasa shagon, wannan karon a buɗe yake, ta tsaya a gefe har mutum biyu da suke ciki suka gama, sannan ta ƙarasa da murmushi ta gaishe shi, ya amsa babu yabo babu fallasa, ta miƙa masa abincin ta ce"Ga shi, ka yi haƙuri na kawo a makare, tun kafin sha biyu na kawo maka, sai na tarar shagon a rufe, na jira wajan minti goma sha biyar sannan na koma saboda su Afna kar su dawo babu kowa". "Ok, na je kasuwa ne" Ya faɗa bayan ya gama jinta. Har ta juya ta tafi ta dawo ta ce"Kenan kullum daidai wancen lokacin kana kasuwa?" Ya ce"Ba kullum ba". Ta ce"Me zai hana ka ba ni lambarka, idan zan zo sai na dinga tambayarka ko kana nan, ko kuma ranar da ba ka nan ka kira ni ka faɗa min ko?" Ya ɗan yi jimm, sai kuma ya ga tana da gaskiya, hakan zai fi mata sauƙi, ya miƙa mata wayarsa ta saka lambar, tana ce masa"Kursum, na san ka manta sunan" Ta ƙarasa da shegen murmushi. Tana fita ya yi saving lambar, sannan ya ɗakko abincin ya fara ci, cokali ɗaya ya yi, ya ji girkinta ya bambanta da na Yusra, ɗanɗanon ba ɗaya ba ne, sai ya bar shi a kowa da irin hannunsa, amma abincin ya yi masa daɗi, ya cinye tass ya sha ruwa. Kursum ba ta jima da komawa ba Yusra ta dawo, dama ta wanke fuskarta kafin ta dawo, kuma ta ƙara wanke-wanke ta gyara gidan tsaf har da turaren wuta, Yusra ta ji daɗin yadda ta tarar da gidanta, a ranar farko har ta fara jin daɗin ɗaukar ƴar aiki, yanzu da tuni yadda ta dawo a gajiyen nan aikin gida za ta hau da girki, yanzu kuwa Kursum na tafiya abinci ta zubo ta ci, ta yi wanka ta kwanta ta huta, sai la'asar ta tashi don tafiya kemis. A shagon shi ta tsaya ta shiga da sallama murmushi ɗauke a fuskarta, ya yi mata murmushin shi ma yana amsawa "Kin dawo?" Ya tambaye ta. Ta ce"Ga ni kuwa, ta kawo maka abinci ko?" Ya gyaɗa mata kai. Ta ce"Na ga alamar za mu shirya da yarinyar, ba ta da son jiki, har da kayan yara ta wanke, gida fess". 'Kuma ta iya girki' Ya faɗa a zuciyarsa. A fili kuma ya ce"Madallah! Kemis za ki je?" Ta ce"E, zan ɗan leƙa, Nura yana can, da wuri ma zan dawo na yi maka tuwo". "To na gode, sai na dawo" Ya faɗa yana ta kallonta, har ta tafi. Ana kiran sallar magriba ta koma gida sai da ta ɗakko yaran a maƙota suka shiga tare, ta ɗora tuwo ta yi alwala suna idar da sallah suka fara bata labarin Anti Kursum, kamar yadda ta ce musu sunanta hakan, ta ji daɗi sosai da yaran suka saki jiki da Kursum ɗin, har ta kira Sumayya ta ba ta labari ta sake yi mata godiya sosai, Sumayya ta ce "Babu komai, ai yi wa kai ne" GIDAN HARUNA Sosai Haruna ya yi mamakin yadda Zainab ta ƙware, ashe karuwar gida ce zaune, duk da babu wani gyara a jikinta amma salonta ya gigita shi, da ƙyar ya bari ta koma ɗakinsu, don roƙonta ya dinga yi ta kwana a nan ɗin, ta ce ba zai yiwu ba, Baaba tana farkawa fitsarin dare, haka ya kwana ransa fess shi bai ƙi Halima ta yi wata ɗaya a gida ba ma. Washegari da safe Halima ta kira shi suka gaisa sai ya ji bai kyauta ba, don tun da ya kai ta gidan bai kira ta ba, ya ce"Ki yi haƙuri Halima wayata ce babu kati, shi yasa ban kira ki ba, ya jikin naki?". Ta ce"Babu komai, jiki Alhamdulillah, yanzu za mu je asibiti da Umma". Ya ce"To Allah Ya ƙara afuwa, da daddare zan zo, Allah Ya sa dai na samu abin da zan siya miki wani abun". Ta ce"Amin, idan ba ka samu ba ma ka zo, zuwan naka ya fi muhimmanci fiye da abin da za ka kawo, ka ga idan ba ka zo ba Umma ba za ta ji daɗi ba". Ya ce"Zan zo in sha Allah! Na gode Halima Allah Ya ƙara miki lafiya, gaskiya zan yi kewarki kafin ki dawo". Ta yi murmushi ta ce"In sha Allah ba zan fi kwana uku ba ai". Gabansa ya faɗi, shi da yake fatan ta yi wata ɗaya sai ga shi tana zancen kwana uku? Ya ce"Haba Halima lafiyarki tana da muhimmanci a gare ni, saboda haka ki zauna ki warware sosai, babu komai zan jure kewarki". Ta ce"To, sai dai yadda ta yiwu". Da daddare da ya dawo daga kasuwa, ya sayi lemo, kankana, madara, milo ƴan saches, suga biredi da maltina ya haɗa da dubu biyu ya kai mata, bayan sun gaisa ta ce"Ga shi ba ni da lambar Zainab ballantana na ji ko tana fita a abincin nata?" Cikin suɓutar baki ya ce"Ai ina da lambarta". Da mamaki ta ce"Lambar Zainab ɗin? Yaushe ka karɓa?" Sai yanzu ya san kwaɓar da ya yi, nan take ya fara in'inar da bai san yana da ita ba. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 2526907490 Aisha Abdulrazaƙ Zenith bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS PAGE 7 Follow the AUTAR MANYA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Ya ce"Na yi zaton Salma kika ce ƙanwarki, ban ji sosai ba". Ba ta kawo komai ba a ranta, suka yi sallama ya tafi. A ranar ma haka Zainab ta je ɗakinsa suka ƙara haɗuwa. Sanda ta kwana uku a gida Baaba ta ce masa ya yi musu kwatance za su je gidan, sai ya kwatanta musu ya kuma ba su lambarta, suka je suka duba ta, Baaba ce take cewa Umman Halima"Tun da jikin nata da sauƙi ai dama komawa ta yi, kin ga Zainab babu abin da ba za ta yi mata ba, ni kuma zan dinga saka ido akanta". Umma ta ce"Gaskiya ne, mun gode Baaba, to in sha Allah ko gobe sai ta koma, ai jikin nata da sauƙi kam, aman ma ya tsaya". Sun ɗan jima suna fira sannan suka tafi, takaici kamar ya kashe Zainab ganin Baaba ta dage sai Halima ta dawo sai kace ita take aurenta, suna hanya ta ce"Wai ni Baaba me yasa kika damu sai ta koma? Ko mijinta bai damu ba sai ke?" Baaba ta ce"Kar ki ishe ni da shirmen banza da na wofi, shi mijin nata ne ya faɗa miki bai damu ba?" Daga haka aka yi shiru da zancen, har suka ƙarasa gida Zainab ranta a ɓace. Ranar ce masa ta yi ba za ta je ɗakinsa ba ma, tun da har ya yarda Halima ta dawo bai damu da ita ba, gara ta yi zamanta, ya dinga rarrashinta ta ƙi sauraronsa. GIDAN ALI Sai da ya yi kwana uku bai je gidan Hajiya ba, duk yadda take kiransa kuwa, saboda ba ya so su sake samun matsala da Maryam kwana kusa, yanzu ana yin sallar magriba yake dawowa gida, kwana uku bai yi zaman majalisarsu ba, sai dai a ganin Maryam an gudu ne ba a tsira ba, tun da kullum sai Hamza ya biyo shi gidan, su zauna a ƙofar gida sai su kai ƙarfe tara, ganin an jera kwana uku a haka ya sa ta fara yi masa ƙorafi, ta ce gaskiya Hamza ya daina zuwa yana hanata fira da mijinta, Ali ya ce shi dai mutum ba zai zo wurinsa ba ya kore shi, watarana Hamza ya zo, Maryam ta tashi ta tare hanya tana haɗe gira, da mamaki Ali ya ce"Maryam mene ne hakan? Ba ni hanya don Allah" Ta ce"Babu inda za ka fita, ka faɗa masa kana buƙatar ganawa da matarka shi ma ya tafi wurin tasa matar". Ali ya ce"To ai shi yanzi ya saki matarsa, shiyasa idan ya koma gida da wuri sai daren ya yi masa tsayi, kuma kin ga nine dai abokin, dole wurina zai zo, na ga nan a ƙofar gida ne kina leƙowa ma za ki ganmu". Ta ce"Idan na ganku zan jiyo irin huɗubar da yake yi maka ne? Wato ya saki matarsa kai ma yana yi maka huɗubar ka saki taka ku zama ɗaya ko?" Ali ya ce"Subhanallah! Haba Maryam wannan wace irin magana ce?" Ta ce"To ni dai ban amince da wannan sabuwar majalisar ba, saboda haka ka faɗa masa ya daina zuwa ba ka so!". Ali ya ce"Wallahi ba zan iya korar shi ba". Ta ce"To wannan abokin naka ya zama kishiyata, saboda haka daga yau ka fara raba mana kwana, ranar kwanana ana magriba ka dawo gida, ranar kwanan shi ana magriba za ka dawo ka tarar da tabarma a ƙofar gida, don ba zan iya ba!". Cikin takaici Ali ya ce"Wai me yasa kike haka ne? Gabaɗaya kin kanainaye ni, sai ka ce ke ce mijin, na faɗa miki shi kaɗai ne a gidan shi ya saki..." "Ya je ya hau sallaya ya fuskanci alƙibla!" Ta katse shi har da ɗaga murya. Ya juya zai fita, ta ruƙo rigarsa ta dawo da shi, ya ce"Maryam wai mene haka?" Ta ce"Da gaske fa nake wallahi, ka bari ni na je na same shi na faɗa masa ina buƙatar mijina a kusa da ni". Ganin ta shiga ta ɗaki ta ɗakko hijjabi Ali ya ce"Bari na je na faɗa masa". Ya fita, bai jima ba ya dawo yana ɓata rai, har lokacin tana tsaye da hijjabin a hannu, ya ce"To ga ni sai ki kwaɗa ki cinye. Ta yi dariya ta ce"Ni da ana kwaɗon ma ai da tuni na cinyeka na huta da matsalolin da kake tara mini". Daga haka suka shiga ɗaki, har ta kunna kallo ya kashe yana cewa"Wucewa za ki yi mu je mu kwanta, ai tun da kin hana ni fita dole ki rage mini daren". Nan take fara'arta ta ɗauke, ta ce"Ni fa tun rana nake jin kasala da ciwon kai, kitso ma yau mutum ɗaya na yi wa". Ya taɓe baki ya ce"Ai wallahi ko karkarwar zazzaɓi kike sai kin wuce mun tafi ɗaki, ai tun da kika kafa mini doka na yi miki sam'u wa ɗa'a ni ma dole ki bi tawa doka, ni wannan dokar ma ai gana ta kai ni gobarar Titi a Jos, babu zancen cewa kin fara bacci, idan da rabo ma sai ki ga cikin satin nan Allah Ya kawo mana babban rabo, kya samu ɗan tayin fira nan da wata tara ko?" Ko kallonsa ba ta yi ba, ta yi shiru kamar ruwa ya cinye ta, fargaba duk ta addabe ta, sai ta ji da ta sani ma ta bar shi da Hamzan, haka dai ta miƙa kai kamar ta yi kuka don takaici. Kwana uku suna yin haka, Maryam gabaɗaya dauriyarta ta ƙare, saboda haka ta fara ƙaryar rashin lafiya, kafin ya dawo sai ta shige bargo ta ce zazzaɓi take yi. Ana haka ne kuma Hajiya ta dame shi da kira kan ya kamata ya zo ko awa ɗaya ne, to shi ma ya yi kewarta, kawai yana dannewa ne ganin yanzu yana yi wa Maryam fin ƙarfi, to da ya ga ta narke da zazzaɓin da ya san na ƙarya ne sai ya ƙyale ta, ya yanke shawarar zai je gidan Hajiyar yau. Yana idar da sallar magriba ya kira Hajiya ya faɗa mata ga shi nan zuwa, ya kama hanya ya tafi, yau ma da kanta ta shigar da shi, kafin su ƙarasa ɗaki yake ƙara kallon gidan, ya ce"Hajiya wai duk girman gidan nan babu mai gadi ne?" Ta ce"Akwai mai gadi, aikensa nake yi idan zan yi baƙo". Ya ce"Kenan dai Hajiya akwai wasu baƙin bayan ni". Ta ruƙo hannunsa a lokacin da suke ƙarasawa ta ce"Wallahi tun ranar da ka fara zuwa har yau na kasa sake kula wani, kai na musamman ne Aliyyu, ni fa da za ka dawo gidan nan da zama gabaɗaya wallahi zan so haka, kana ɗaki kawai a cikin AC, ka zaɓi abin da za a dafa maka ka ci ka kwanta, sannan kullum dubu goma". Ya yi ƴar dariya ya ce"Kin ga kuwa da har ƙiba fa sai na yi". Hajiya ta ce"A to! Ka dai duba wannan damar". Ya sosa kai ya ce"Ai Hajiya matata nake tunani, kin san fa amarya ce ko haihuwar fari ba ta yi ba, kuma wallahi tsaye take a kaina, tana lura da duk wani motsina, shi yasa amma da ni ma zan so hakan wallahi". Hajiya ta ce"To kai kuwa Aliyyu ya aka yi ka yi sake matarka take juya ka har haka? To me zai hana ka ce mata ka samu aiki a wani garin, sai ka zo mu yi zamanmu, duk kwana biyu ka dinga tura mata kuɗi ka kashe bakinta, ko ba zai yiwu ba?" Aliyyu ya ce"Kuma fa kin kawo shawara Hajiya, zan yi tunani, ke zai yiwu ma in sha Allah!". Ta ce"Ko kai fa, na gode, sosai nake sonka Aliyyu, ji nake kamar na kashe auren nan na aureka wallahi". Ya yi murmushi ya ce"Habawa Hajiya wane kare da ɗaukar gara? Wani kayan ai sai amale". Daga haka ta kawo masa abinci ya ci, ya yi wanka, ya fara abin da ya kawo shi, ƙarfe tara ya baro gidan, yana ta sauri saboda Maryam, a hanya ya tsaya ya kira ta, tana ɗagawa ya ce"Maryam ki yi haƙuri ga ni nan zuwa". Ba ta ce komai ba ta kashe, sai da ya tsaya a hanya ya siya mata kwakwa da dabino sannan ya ƙarasa gidan. Yana zuwa ya ganta fuskar nan kicin-kicin. Ya yi murmushi ya ce"Hajiya Maryam kenan, uwargidana amaryata, sarautar mata daga ke babu ƙari..." Ta ɗaga masa hannu ta ce"Don Allah dakata, ya isa haka, na san dai duk siyan baki ne kake yi, babu komai Ali duk yadda ka tsara rayuwarka ka je ka yi ta yi, ni dai Allah Ya sani na yi iya ƙoƙarina don na ga na kula da kai, tun da kana ganin kamar takura ne shi kenan, ka je ka yi". Ya zauna, ya janyo ta jikinsa, yana cewa"Haba Love, wallahi ba takura ba ne ba, na sani ƙauna ce, kuma ina jin daɗin yadda kike kulawa da ni ɗin wallahi, yanayin aiki ne kawai, ga kwakwa na kawo miki, na san za ta wanke laifina ai ko?" A zahiri shi take kallo, amma sam ba ta gane inda maganganunsa suka dosa, ta yi nisa a duniyar tunanin da zuciyarta ta ɗarsa mata, dalilin kusancin da suka samu, sakamakon zamanta a cinyarsa, wani kalar ƙamshi ta ji na wata shegiyar humra mai daɗin ƙamshi, kuma ta san Ali idan zai fita da safen nan ba ya wani fesa turare ma, ko ma yau ya fesa ai ba su da irin wannan turaren, kuma ma fa wannan humra ce, kamar ta yi masa magana, sai ta bar shi a kan za ta yi bincike kafin ta tuhume shi. GIDAN SADIQ Rayuwar gidan Sadiq ta samu ci gaba a nasu ganin shi da Yusra, yanzu hankalinta ya kwanta sosai, tsakaninta da Kursum sai godiya da fatan alkhairi, idan tana aikin kwana ko fargabar ta bar mijinta da wata a gida ba ta yi, domin ta yarda da su, su biyun, yayinda Kursum matakan da ta tanada don shayar da Yusra maɗaci suke ta tafiya hawa-hawa. A yanzu dai ta riga da ta gama da Sadiq da yaransa wajen girki, ya yarda a kan Kursum ta fi Yusra iya girki, don sosai Sumayya ta kashe kuɗin wurin siya mata kayan ɗanɗanon girki, wanda Yusra duk ba ta san wainar da ake toyawa ba, duk da ƴaƴanta sun sha faɗa mata girkin Anti Kursum yana da daɗi sosai, ita ba ta kawo komai ba, tun da ba ta ji wani bambanci da nata ba. Abu ɗaya ta sani Kursum tana taimakonta. A ɓangaren Sadiq tsakaninsa da Kursum babu yabo, babu fallasa, kullum za su gaisa tana murmushin da ya gane ɗabi'arta ne, sai dai yadda ba ta gajiya da kwalliya abun yana burge shi, saboda shi mutum ne mai son kwalliya sosai, duk da bai taɓa faɗawa Yusra ba tun da ya lura ita ba ta da ra'ayin wannan zane-zanen, sai kuma tsafta da take da ita sosai abun yake burge shi, uwa-uba kuma yadda take kula masa da ƴaƴa, abun sha'awa, sun shaƙu da yaran sosai ba su da zance sai na Anti Kursum ɗinsu, saboda haka shi ma yanzu aikin Yusra ba sosai yake damun shi ba. Sai dai wani baƙon lamari da yake faruwa da shi, wanda tun yana damunsa yanzu ya zame masa jiki, ta wani ɓangaren ma abun ɗebe kewa ne a gare shi. Wata yarinya ce take turo masa massages kala-kala, na kulawa, tun yana sharewa har ta kai ya fara mayar da hankalinsa a kan saƙonninta, duk ranar da ba ta turo ba sai ya yi ta tunanin dalili, akwai lokacin da ta yi kwana uku ba ta tura masa saƙo ba, duk ya kasa sukuni, motsi kaɗan ya duba wayarsa, ranar na ukn sai ya kirata a waya, sosai ta nuna farincikinta, kuma ta faɗa masa ba ta da lafiya ne, jiya aka sallamo ta daga asibiti, kamar wasa tun daga ranar suka fara yin waya da yarinyar da ta ce sunanta Ummu, ta iya kalamai masu tsayawa a rai, sosai yake mamakin kansa, don bayan Yusra bai yi tunanin zai sake iya soyayya da wata ba, sai ga shi cikin sauƙi ya faɗa soyayya da wacce bai santa ba, kuma ko hotonta za ta turo masa sai dai ta rufe fuskarta, to shi ma a yanzu bai shiryawa wani auren ba, shi yasa ya bar ta a je a hakan, amma yarinyar ta yi masa har zuciyarsa, sosai suke waya musamman ranar da Yusra take aikin kwana. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 2526907490 Aisha Abdulrazaƙ Zenith bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN Airtel NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL. [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: *WANI AUREN* BY SADIYA ABDULRAZAƘ FIRST CLASS WRITERS PAGE 8 Follow the AUTAR MANYA CHANNEL channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VakTcGc5Ejy40GSTWA0h *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN HARUNA Ƙiri-ƙiri Haruna ya ƙi cewa Halima ta dawo, duk da ta faɗa masa jikin da sauƙi sosai, ita kuma mahaifiyarta tausayinta take ji, shi yasa ta ƙyale ta ta dinga hutawa, Halima har mamaki take yi yadda kullum idan zai zo ganinta sai ya taho da leda sannan ya ba ta kuɗin kashewa, sosai hakan ya yi mata daɗi, ta fara tunanin mijinta ya fara samu sosai a kasuwa, amma ta saka a ranta duk da haka ba za ta dakatar da sana'arta ba, za ta ci gaba da yi don a taru a rufawa juna asiri. Bayan kwana uku suka shirya da Zainab, har ma suka shirya yau ma za su haɗu a ɗakinsa, don haka da daddare ƙarfe ɗaya Zainab ta tashi saɗaf-saɗaf, ta shige ɗakinsa, ta saka sakata, suka fara sha'aninsu, bai fi minti goma da shigarta ba Baaba ta tashi don yin fitsari, ta ji ɗakin a buɗe duk da ta san da kanta ta saka sakata, kuma Zainab ba ta tashi fitsarin dare, sai ta yi tunanin ko yau ta tashi ne tana banɗaki, ganin butarsu a yadda ta ajiyeta ma bai sa ta yi wani tunanin ba, ta ɗauka ta je ƙofar banɗaki ta tsaya tana jiran fitowarta, jin shiru ba ta da niyyar fitowa ya sa ta cewa"Da mutum?" Ta ji shiru, ta bubbuga ƙofar nan ma shiru, sai ta leƙa a hankali tana haskawa ta ga wayam babu kowa, ƙirjinta ya bada sautin rass ta fara tunanin ina Zainab za ta tafi cikin daren nan? Ta shiga ta yi fitsarinta, ta yi zaure ta ga ƙofar gida a rufe tsaf, gabanta sai faɗuwa yake yi, ta dawo ta shiga ɗaki wai ta ƙara dubawa ko idonta ne ya nuna mata Zainab ba ta nan, amma ganin ko bargo babu a kan shimfiɗar ballantana a yi tunanin ta lafe a ciki ya sa ta saddaƙar wani abu ya samu jikarta, tuni ta fara hawaye, zuciyarta tana bugawa. Kamar ta tashi Haruna ta faɗa masa halin da take ciki, sai kuma ta fasa, don tana tunanin samari ne suka hure mata kunne ta gudu bariki, sai ta miƙe zumbur ta shiga ɗaki ta duba kayan sakawar Zainab, ta gansu tsaf babu alamar an ɗauki wani abun, har hijjabin da ta yi sallar isha'i ma yana nan a inda ta bar shi, Baaba ta dawo tsakar gida ta zauna a kujera tana matsar ƙwalla. A firgice ta ɗago jin an buɗe ɗakin Halima, ta miƙe tsaye don ta samu damar da za ta faɗawa Haruna, ya je ya dubo ko ba ta yi nisa ba ya faffalla mata mari ya dawo da ita, sai dai ta yi turus ganin mace ce ta fito, cikin sakan ɗaya ta yi tunanin ko Halima ta dawo tana bacci? Amma ganin wacce ta fito ɗin ta doshi ɗakinta gadan-gadan ya sa ta yi saurin kunna fitarta hannunta na rawa. A firgice Zainab ta juyo ganin an haskata, ƙirjinta ya buga da ƙarfi ganin Baaba ce a tsaye. Baaba kuwa sakin fitilar ta yi, ta dafe ƙirji, cikin razani ta ce"Zainab! Me kika yi a ɗakin Halima?" Cikin inda-inda ta ce"Caji na saka fa Baaba". Baaba ta ce"Bantan ubanki ke da cajin" Sai ta ƙaraso ta rufe ta da duka, kafin ta saketa ta fashe da kuka, ta shige ɗaki. Ita ma Zainab ɗin shigowa ta yi, ta zauna rakuɓe a gefe tana hawayen nadama, can Baaba ta ce"Zainab yanzu shahararki a iskanci ta kai har da na gida? Har cikin gida, da mijin maƙociyarmu? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!". Zainab tana kuka ta ce"Ki yi haƙuri Baaba, wallahi iya yau ne kawai, kuma mun yi na farko mun yi na ƙarshe". Baaba ta ce"Amma wannan yaron an yi ɗan banza, Allah sarki Halima ashe ba ta yi dacen miji ba, kaico! Da halinku ke da shi ɗin, sai Allah Ya sakawa Halima". Sai kuma ta tashi, ta je ta fara ƙwanƙwasa ɗakin Haruna, don Zainab tana fita ya saka sakata, ya yi lakur saboda yana jiyo tattaunawarsu sama-sama, gabansa ya faɗi da ƙarfi da ya ji ana buga ƙofar, kamar kar ya buɗe sai kuma ya daure zuciyarsa ya buɗe, cikin karaya ya ce"Baaba ce da daren nan?" Baaba ta ce"Haruna ka ji tsoron Allah! Ka sani akwai mutuwa, akwai hisabi, sannan zina bashi ce, kuma duk wanda yake cin amanar aure ba zai yi kyakkyawan ƙarshe ba in sha Allah!". Cikin ƙarfin hali ya ce"Mene ne ya faru ne Baaba?" A fusace ta ce"Uwarka ce ta faru da ubanka! Me ya kawo Zainab ɗakinka da daren nan?" Ya ce"Wai Zainab? Wallahi zuwa ta yi, ta ce min wayarta babu kuɗi, na kira mata Halima za ta tambaye ta wani abu, akan sana'ar da take taya ta". Baaba ta ce"Ita kuma ta ce caji ta saka, babu komai Haruna duniya ce ta fi bagaruwa iya jima! Idan ni da Halima muna da hakki akan cutarwar da kuke yi mana Allah Ya saka mana tun a duniya". Daga haka ta shige ɗakinta, ta bar shi riƙe da ƙofa, jiki a mace kamar kazar da ta taka wuƙa ya dawo ya zauna a kujera yana dafe kansa, ya jima a haka sannan ya tashi ya saka sakata ya koma ya kwanta. Washegari safe Zainab ta tashi ta shiga harkokin wainarta kamar ba a yi komai ba, saɓanin Haruna da ya kasa fitowa sai da suka yi chart ta faɗa masa babu komai ya maze kawai, kuma haɗuwa yanzu ma suka fara, ta samo musu wata dabara, wannan ne ya ba shi ƙwarin gwiwa ya saki jikinsa, har ya fice daga gidan. Ita kuwa Baaba ƙarfe goma na safe ta shirya ta tafi gidan su Halima, suka gaisa ta cewa babarta ta zo tafiya da Halima ne, Umma tana murmushi ta ce"Ai Baaba gani na yi har yanzu bai ce ta koma ba, shi yasa na barta ta ƙara hutawa". Baaba ta ce"Haba ƴar nan, ku kuma ai ya kamata ku gane kara ce yake yi, sai ka ce laulayin kanta ne farau? Kuma fa ƴata Halima ai jaruma ce, ni dai yau da ita zan koma gidan nan Allah kuwa". Umma ta ce"To kin ji dai Halima, sai ki tashi ki shirya, bari na je kasuwa na yi miki ƴar siyayya, idan na dawo sai ki bi Baaba ku tafi, ka samu mai kula da lamarinka ma ai abun murna ne, mun gode Baaba". Bayan ta tafi kasuwa suka dinga fira da Halima tana ta jaddada mata ta riƙe mijinta, ta dinga saka ido sosai a kan shi saboda ƴan matan zamani ba su da kirki, a haka har Umma ta dawo, Baaba ta saka ta a gaba suka koma. Ita kanta Baaba sai da ta yi mamakin yadda Zainab ta nuna ko a jikinta, ita ta gyara mata ɗakinta fess tana ta yi mata sannu. Haruna bai san da dawowarta ba, da yake akwai mukulli a hannunta, sai dawowa ya yi ya tarar da ita, ya ɗan ji daɗi saboda dama yana shakkar dabarar Zainab duk da shi ma ya san ba abu ba ne mai sauƙi yadda ya saba da ita su rabu lokaci ɗaya, amma tun da Baaba ta san komai ya zama dole su canza taku idan ma za a kuma ɗin, da wannan ya saki jiki da Halima har suka taɓa fira kafin ta yi bacci. GIDAN ALI A cikin satin Ali ya zowa da Maryam sabon labari, na cewar wani kamfani a can Enugu zai ɗauke su aiki na sati ɗaya, kullum dubu goma, kuma su ne za su yi musu kuɗin mota,masauki da abinci bakiɗaya, ganin ta ɓata rai ya sa shi tausasa murya ya ce"Maryam don Allah idan na zo mana da abun alkhairi ki daina gwasale ni, ki dinga yin fatan alkhairi kawai, kwana bakwai fa kacal za mu yi, dubu saba'in ina laifi? Ba sai na yi miki kayan sallah a ciki ba?" Ta ce"Ni fa ba aikin ne ba na so ba, garin ya yi nisa, kuma har kwana bakwai". Ya ce"To ai haƙuri za ki yi, wanda ya tashi nema ai ba ya duba nisa Maryam, ni ma zan yi kewarki kuma na akwai masu tafiya su yi wata bakwai, ko shekara bakwai, to ina laifi don na yi kwana bakwai?" Ta ce"Haka ne, shi kenan Allah Ya kai ka lafiya, ya dawo mini da kai lafiya, Allah Ya ba da abin da aka je nema". Ya ce"Amin mace ta gari, ko kefa! Amma da kin tsaya kina wani tantama? Gobe da yamma za mu tafi, saboda haka yau kam duk rowarki sai kin bar min daren nan duka, kya dinga tunawa da ni ko?" Ta ce"Kai ai aikinka kenan, na rasa me kake ji, ni dama tun can babu wannan abun a aure da na ji daɗina" Ta juya kai gefe Ya ce"Maryam kenan, ke dai na rasa irin tunaninki wallahi, nan gaba za ki saba dai, ina ga sai kin haihu ko?" Ba ta ce komai ba, ta tashi ta kwashe kwanukan da suka ci abinci. Kafin ya shigo ɗaki ta yi luf kamar mai bacci, saboda fargabar furucinsa ta kasa baccin ma, ya yi abin da zai yi ya kwanta, yana kai hannu jikinta, ta ce"Na fa fara bacci, ga ciwon kai". Ya matsa gefe, don dama ba wai buƙatarta yake yi ba, kawai dai don ta sake yarda da tafiyar tashi ce, shi da zai je ya ɓarje guminsa a gidan Hajiya har ya tsaya ana kace-nace da shi? Daga haka ya juya ya fara baccinsa hankali kwance, har zumuɗin zuwan goben yake yi. Washegari bai fita aiki ba, da kanta ta haɗa masa kaya a jaka, har ta ce ya siyo fulawa ta yi masa cincin ya ce a'a ta bar shi, tun da kanta yana ciwo, tun azhar Hajiya ta yi masa tex ɗin tana ta jira, ya ce mata sai da yamma, ana idar da sallar la'asar ya ɗauki jaka yana yi wa Maryam marayan kallo saboda yaudara, sai ya ga ta tashi ta saka hijjabi, ya ce"A ina zuwa kuma?" Ta ce"Ai ya kamata na raka ka tasha ko?" Ya ce"Haba Maryam wace tasha kuma? Mu da za mu haɗa da yawanmu a ƙasan layi sannan mu ɗunguma zuwa tasha, kuma tsakani da Allah sai a ce ni ne kaɗai matata ta rako ni?" Ta ce"To mene ne idan ma an faɗa?" Ya ce"A'a wallahi ni dai ina kishin a gane mini kyakkyawar matata, duk sallamar da za mu yi mu yi ta a iya zaure, kwana bakwai ne fa, kamar yau ne, yi haƙuri kin ji?" Haka dai ya lallaɓata ya tafi, bai samu nutsuwa ba sai da ya gan shi a gidan Hajiya, sosai take farin ciki da zuwansa, jinta take tamkar wacce ta yi sabon aure, ɗakin mijinta ta buɗe ta kai kayansa ciki, ta faɗa masa nan ne masaukinsa, tun kafin ya zo ta sallami ƴar aikinta, ta ce mata tafiya za ta yi, sai bayan sati ɗaya idan ta dawo za ta neme ta, saboda haka da kanta ta yi masa girki sakwara da haɗaɗɗiyar miyar da ta zuba yajin maza a ciki ta yi lafiyayyen kunun aya shi ma ta watsa masa ƙwayoyi, Aliyyu ya kwashi abinci ya yi wanka, suka fara shagalinsu, bayan ya kashe wayarsa. Bai kunnata ba sai washegari shi ma sai azhar, don sosai ya kwashi ramuwar bacci da safe, ya kira Maryam suka gaisa yake faɗa mata yanzun nan suka sauka, ta ce"Alhamdulillah! Tafiya ta yi kyau, ina ta tunani wayarka na kikkira a kashe ashe sai yanzu kuka je, amma dai da nisa". Ya ce"Ke dai bari Love, kwana muka yi a hanya, ana sharara gudu, sai yanzu muka isa". Ta ce"Ma sha Allah! Da daddare za mu yi chart". Hajiya dake zaune tana jin duk wayar tasu, ta kaɗa masa ɗan yatsa alamar a'a, tana maƙe kafaɗa kamar yarinya. Ya ce"Ai Maryam chart dai yau ba zai yiwu ba, jiya fa ban yi bacci ba, yanzu caji zan bada wayata, a kaimu mu ga yanayin aikin, sai mu ci abinci a kaimu masauki, kin ga ina yin wanka sai bacci, tun da gobe sassafe za mu tafi wurin aikin". Cike da tausayawa ta ce"To Allah Ya tsare ku, Ya ba da sa'a Love ka kula da kanka sosai don Allah, ban da kai wa dare a waje ka ga dai ba ka san kowa ba". Ya ce"Haba ina ma na ga wannan damar? Mu da za mu wuni aiki, ai ina dawowa sai bacci, ke ma sai dai ki yi haƙuri ba za mu dinga doguwar waya ba". Daga haka suka yi sallama, ya kalli Hajiya yana washe baki, ta juya kai ta ce"Ina kishi da wannan matar taka gaskiya". Ya ce"A haba Hajiya, ai kin wuce ki yi kishi da Maryam". Ta ce"Ba ni labarinta, tana sonka sosai ko?" Kamar ta yi masa allurar tonon silili haka ya ɓarke ya fara ba ta labarin Maryam, hatta gidan iyayenta da yadda suka fara soyayya zuwa aurensu, da sana'ar da take yi, duk sai da ya faɗa mata, sannan daga baya ta nemi sanin unguwar da yake haya, ya kwatanta mata tsaf. Haka rayuwa take gudana tsakanin Hajiya da Aliyyunta, suna ɓarje soyayya, Ali sai dai a ci a sha a kwanta a yi bacci, daga shi sai gajeren wando za ka gan shi a falo yana kallon TV, AC tana ratsa shi, ya shiga kitchen ya yi ciye-ciyensa son ransa, kullum ya ji alert ɗin dubu goma. Kwanansa biyar a gidan, Hajiya ta ce masa za ta je unguwa, tun da ya zo bai ga ta fita ba sai yau, tana yin baƙi, idan za su zo sai dai ta ya shige ɗakinsa ya yi kwanciyarsa. Kai tsaye Hajiya ta bi kwatancen da ya yi mata, ta je har gidan Maryam, a buɗe ta tarar da gidan, ta yi sallama ta shiga, ta tarar da mata guda biyu suna fira, wanda kwarjinin Hajiyar ya sa suka yi zaton wata babbar baƙuwa ta yi, suka yi wa Maryam sallama suka tafi, Maryam ta tashi tana yi mata sannu da zuwa, Hajiya ta ja kujera ƴar tsuguno ta zauna ta ce"Yawwa Maryam, dama kitso na zo ko zan samu?" Ta ce"Za ki samu, bari na ɗakko tabarma". Ta shiga ɗaki, Hajiya ta bi bayanta da wulaƙantaccen kallo, ta fito ta shimfiɗa hannunta riƙe da kibiya ta ce"Bisimillah". Hajiya ta zauna a tabarma, Maryam ta fara yi mata kitso, tana ji ta ɗakko wayarta ta yi kira, ta ji tana cewa"Ali na samu gidan Maryam ɗin, ga shi nan ma har ta fara yi mini kitson". Can kuma ta ce"A babu komai wallahi, tana da kirki, bari dai idan na zo gidan ma yi magana". Maryam ta ɗan yi mamaki jin irin sunan mijinta kuma da alama mai sunan ne ya kwatanta mata har ta zo kitson, ba ta kawo komai ba har ta gama yi mata, Hajiya ta ɗauki dubu biyu ta bata, Maryam ta ce"Ai baiwar Allah bai kai haka ba, ungo kuɗinki har dubu biyu?" Hajiya ta ce"Haba ai yiwa kaine, ke da Ali ai duk ɗaya kuke a wajena". Cak Maryam ta tsaya ta ce"Wai wane Alin?" Ta ce"Ba sunan mijinki Ali ba, wanda ya yi miki ƙaryar ya tafi Enugu aikin kamfani? To idan ya dawo ki faɗa masa Hajiya Zuwaira tana gaishe shi". Daga haka ta fice tana murmushi, ta bar Maryam wacce mamaki ya daskarar da ita. Shi kuwa Ali yana falo ya yi ɗai-ɗai yana kallo a TV, lokaci-lokaci yana damƙar dambun nama yana ci, ya ga an buɗe ƙofa, da sauri ya miƙe tsaye ganin wani mutumi ne ya shigo ba Hajiya ba, kallon-kallo suka shiga yi da mutum, kafin Ali ya kwasa a guje ya yi hanyar ɗakinsa, mutumin ya bi sa ya guje yana cewa"Waye kai!?" Ali ya murɗa key zuciyarsa tana bugawa da mugun ƙarfi, ga shi ya bar wayarsa a falo. GIDAN SADIQ Yau ta kasance Asabar Yusra tana gida, don haka Kursum ba za ta zo ba, bayan ta gama duk ayyukan gida ta kwanta tana bacci, har ta makara sai da aka fara kiraye-kirayen sallah ta farka, ta fito ta ɗora girki, tana gamawa ta zubawa yara, suna yin cokali ɗaya suka kalli juna, Afna ta ce"Ni dai Momy na ƙoshi" Fanan kuma ta ce"Momy me yasa abincin Anti Kursum ya fi yin daɗi?" Da mamaki Yusra take kallonsu, ta ja abincin ta yi cokali ɗaya ta ji babu wata matsala, ta ce"Ita na Anti Kursum ba irin wannan ba ne?" Afna ta ce"Nata ya fi daɗi, kuma da wuri take gama yi mana, ta ba mu a baki". Yusra kanta ya kulle tana kallon abincin ta ce"Mene ne bambancinsu?" "Yara ma suka gane ballantana ke? Haba Yusra yanzu za ki ce duk tsawon lokacin nan ba ki gane canjin ɗanɗanon abinci da aka samu ba a gidan nan sanadin Kursum?" Sadiq ya faɗa wanda ba su san da shigowarsa ba Cak ta tsaya tana kallonsa da auna maganganunsa, ya ce"Wannan ba wani abun mamaki ba ne, kin san an ce dama kowa da irin hannunsa, ni ɗakko min abincina na koma, yunwa ce ta dawo da ni, Kursum kafin sha biyu take kai min abincina har na saba da ci da wuri, ke kuwa sai ƙarfe biyu, duk yunwa ta gama cinye mutum". Ai Yusra ji ta yi kamar an zare mata laka saboda tsananin mamaki, ba ta gama tsinkewa ba sai da ta ga ya shiga kitchen ya ɗakko abincin ya zauna zai fara ci, ta tashi ta je ta tankwaɓe cokalin hannunsa abincin da ya ɗibo ya zube, ya ɗago yana yi mata kallon mamaki, ta ce"Abincin da babu daɗi za ka ci? Ai sai ka jira Kursum ɗin ta dafa maka! Wai da gaske ni kake faɗawa wata ta fi ni iya girki?" Sadiq ya ce"Yaushe kika ji na ce haka? Don na ce an samu canjin ɗanɗano ba shi yake nufin nata ya fi daɗi ba, shekararmu nawa da nake ina cin abincinki? Idan ba ya yi mini daɗi za a kai wannan ranar ban faɗa ba? Inda kin zauna kina sauke hakkin gidanki ta ya ma Kursum ta kai na ci abincinta?" Ya faɗi hakan, don kuwa bai ga abin da zai sa ya yi sake Kursum ta bar gidan nan ba, don ko ta fannin girki kaɗai an samu ci gaba, shayi ma wannan idan ta dafa sai ya ji bambanci da na Yusra. Ta ɗan ji dama-dama a zuciyarta ta ce"Amma ai ka ce ita da wuri take kai maka abinci, mai yasa za ka yabeta?" Ya ce"Dole fa idan an yi min na faɗa, kullum ba kya kai min abinci sai kun gama ci ke da yara, ita kuwa kafin sha biyu ta gama ta kawo min". "Hmm!" Ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta ɗakko masa wani cokali ta koma ɗakinta ta zauna ta yi shiru, ba don tana son Kursum ba da babu abin da zai hana ta canzo wata, don ta san mijinta ba akan komai yake mayar da hankali ba, tun da ya fara wannan ƙananun maganganun akwai dalili, amma koma mene ne ta saka a ranta za ta fara kula. Daddare yana falo yana chart da Ummu, wacce take ta ce masa ya je ya kwanta yau Anti tana gida, shi kuma sun ɗakko maganar da ba ya so a katse, kwatsam sai ji ya yi an warce wayar hannunsa, ya ɗaga kai ya kalli Yusra wacce bai ji ko motsin fitowarta ba, da sauri ya kai hannu zai warce wayar ta riƙe ta ƙam cikin hargagi take cewa"Sadiq wace ce Ummu? Wace mai tsautsayin ce ta shigo mini rayuwata!? Sadiq!" Ransa a ɓace ya ce"Malama ba ni wayata". Tana huci tare da zazzare ido ta ce"Ba zan bayar ba!". Ya ruƙo ta, sai ga su suna kokowa har ya ƙwace wayarsa ya shige ɗaki, ya barta durƙushe a falo tana kuka. Zama ya yi a bakin gado ya dafe kansa, yana tunanin bai kyauta mata ba, sai dai wata zuciyar tana faɗa masa hakan ba komai ba ne, tun da ba haramun ya aikata ba, shi kam a yadda yake jin Ummu a cikin zuciyarsa babu me iya raba shi da ita, kuma ya ma saka a ransa ya zama dole ya nunawa Yusra ba yana ƙin kula mata ba ne saboda tsoron kishinta ko kuma ba shi da niyyar ƙarin auren ba, saboda haka dole a cikin satin nan ya san wace ce Ummunsa, kuma su daina wasan ɓuyan nan su fuskanci juna, kowa ya san the game is over. To fa! Kuna tunanin idan Sadiq ya san wace ce ɓoyayyiyar masoyiyarsa zai ci gaba da sonta? Sannan ya Yusra za ta yi idan auren ya tabbata? Ga dai Ali nan an tarfa shi a cikin gidan Hajiya, yana da hanyar fita? Ƙwan da Hajiya ta kai gidan Ali idan ya fashe ya za a kwashe tsakanin Ali da Maryam? Halima ta dawo, yaya alaƙar Zainab da Haruna za ta kasance? Shin dabarar da ta ce ta samu za ta kai musu kuwa? LAST FREE PAGES! ƳAR'UWA KI SIYA KI KARANTA CIKIN AMINCI, YANZU AKA FARA TAFIYAR LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Aisha Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN AIRTEL NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 ALI Duk ilahirin jikin Ali rawa yake yi, tamkar an kunce masa notuna, sai salati yake yi cike da fargaba da nadama, yau ya kawo kansa ga halaka, jin shiru mutumin bai yi wani motsi ba, ya sa Ali tunanin yanzu haka ya tafi kwaso ƴan sanda, ko mazan unguwa a taru a yi masa ihun kwarto, ya jima a haka a ransa yana ta fatan Hajiya ta dawo ta san wannan musifar da suka shiga "Allah sarki Maryam, kin ga hakkinki ya damƙe ni tun kafin a je ko'ina, kaicona, yau ce rana dubu ta ɓarawo..." Jin ana buga ƙofar ɗakin, ya zabura ya fara karanto La haula wa la ƙuwwata illa billah, sai maimaitawa yake yi babu ƙaƙƙautawa zuciyarsa kamar za ta fasa ƙirjinsa ta fito. "Kai ƙaramin ɗan iska ka buɗe! Yau ƙarshenka ya zo" Mutumin ya faɗa da ƙarfi, wanda hakan ya sa Ali ya ɓarke da kuka, jin ana ƙoƙarin buɗe ƙofar da mukulli ya sa shi zabura ya shige banɗaki ya saka sakata, yana ta kukan nadama. "Aliyyu ka buɗe ƙofar nan mana". Hajiya ta faɗa tana buga ƙofar banɗakin, sai ya ji dama-dama, tun da dai koma mene ne yanzu ba shi kaɗai ne a hannu ba, har da ita, ya ce"Hajiya yau mun shiga uku, na yi nadama wallahi". Dariyarta da ya ji ne ya tsaya cak yana mamaki, ta sake cewa"Haba Aliyyuna kana cikin aminci ka buɗe". Sai a lokacin ya yarda, ya buɗe ya fito, fuska kaca-kaca gumi da hawaye, Hajiya ta kalle shi ta saka dariya, mutumin ya ce"Wuce Malam Aliyyu yau a bayan kanta za ka kwana!". Hajiya ta kai wa mutumin duka ta ce"Ba na son wulaƙanci fa, duk ka firgita mini shi, sorry Aliyyu" Ta ƙasara tana janyo hannun Alin, wanda ya kasa gane abin da yake faruwa, shi dai cogewa ya yi ya ƙi fita daga ɗakin, Hajiya suka fita ita da mutumin, babu jimawa ta dawo, yana zaune a bakin gado har yanzu bai nutsu ba, ta ce"Aliyyu ka saki jikinka mana, haka kake da tsoro?" Ya ce"Haba Hajiya, ta ya zan saki jikina bayan ban san wane ne wannan mutumin ba? Ni fa na yi zaton mijinki ne wallahi". Tana dariya ta ce"Kuma idan shi ne sai ka gudo ɗakinsa? Daɗin kama ka kenan ma". Ya ce"To wane ne?" Ta ce"Wani ɗan'uwana ne fa". Ali ya ce"An gudu ba a tsira ba! Yanzu idan ya je gidanku ya faɗa fa? Ni dai Hajiya bari na haɗa kayana na tafi". Hajiya ta ce"Babu komai fa, ai ya saba zuwa ya tarar da irin hakan, kwaɗayinsa ne yake kawo shi, inda zai tona min asiri da tuni ya daɗe da yin hakan". Ali ya ce"Shi ne ya tsorata ni har da biyo ni da gudu?" Hajiya ta yi dariyata ce"Yana sane, ce min ya yi ya zata kai ɓarawo ne, tsorata kawai ya so yi, manta da shi". Daga haka Ali ya shiga banɗaki ya yi wanka, ya saka kaya ya fito falo, a kitchen ya hango ta, sai ya zauna a falon ya ɗauki wayarsa, ya kira lambar Maryam ta ƙi shiga, ya kwanta yana jin rashin nutsuwa don kuwa wannan abin da ya faru yau idan mijinta ya yi mata dawowar bazata hakan ne zai sake faruwa, saboda haka gara ya tafi, ya dinga zuwa ba dai kwana ba. A ɗarare ya ƙarasa sati ɗayansa, ga damuwa na rashin samun Maryam a waya, bai san halin da take ciki ba, don haka ranar tafiyar shi tun safe ya ce wa Hajiya zai tafi, ta ce"Haba dai, yanzu idan ka koma da safen nan ai sai ta ce yaushe ka taho da har ka ƙaraso da wuri haka? Sai dare za ka koma, me da me zan siya maka na tsaraba? Kuma me zan yi maka na snacks? Na ga kana son ciye-ciye". Ali ya ce"E kuma fa haka ne Hajiya, to bari na bari sai daren, ki yi min dambun nama wallahi na saba da shi sosai". Ta yi dariya ta ce"To zo mu shiga kitchen ina aiki ina kallonka ina jin sanyi a raina, sai na fi sauri, na ba da kuɗi ma anjima za a kawo maka kayan sakawa fa". Ya washe baki ya ce"Ina godiya Hajiya Allah Ya saka miki da alkhairi". Ta ce"Haba Aliyyu wannan ba komai ba ne, indai za ka dinga zuwa kana faranta mini ni kuwa zan yi maka duk abin da kake so, na yaba da hankalinka sosai Aliyyu, maza da yawa da na yi mu'amala da su, sai ka ga kuɗina kawai suke so, wasu su yi ta roƙona, wasu ma su yi mini sata, amma kai dai duk wata jarabawata ka cinye ta, shi yasa na nutsu da kai sosai". Yana murmushi ya ce"Na gode Hajiya, Allah Ya saka da alkhairi". Kafin magriba ya gama shirya komai, ta haɗa masa kaya kala biyar da ta siya masa, da takalma biyu, ga dambun nama, cake, gireba da cincin, sannan ta kwasar masa kayan abinci kala-kala har da kayan shayi, ta ɗora masa leshi mai kyau da mayafi wai ya kai wa Maryam, ta kuma ba shi dubu goma a hannunsa bayan saba'in da take cikin account ɗinsa. Ali har da hawayen farin ciki, ya dinga yi mata godiya da faɗa mata zai yi kewarta, har ƙofar gidansa mai adaidaita sahu ya ajiye shi, lokacin ana kiraye-kirayen sallar isha'i, ya fara ƙwanƙwasawa cike da zumuɗin ganin Maryam. GIDAN SADIQ Yau ce rana ta farko da Sadiq ya ƙyale Yusra ta kwana a falo, wannan halayyarta ce duk lokacin da saɓani ya shiga tsakaninsu za ta tafi falo ta kwanta, shi kuma ba ya taba bari ta kwana zai je ya lallaɓata su shirya a lokacin. Da asuba zai tafi masallaci ya same ta zaune a kan kafet ta kifa kanta a kujera, har ya wuce ta ya dawo da baya ya ce"Ki tashi ki yi sallah asuba ta yi". Wani baƙinciki ya sake turnuƙeta, tana jin fitarsa ta tashi ta shiga ɗakin, don ta san ba ya fita da wayarsa masallaci, sai dai yau tana zuwa ta ga wayam babu alamun wayar, ta riƙe ƙugu tana yin huci mai zafi, sannan ta yi alwala ta yi sallah ta kwanta, bacci mai nauyi ne ya ɗauke ta har yara suka tashi suna jin yunwa, kamar ya yi musu girkin sai kuma ya fasa, ya shiga ɗakin, yana bubbuga fulon da take kwance ya ce"Malama ki tashi ki sallame ni zan fita". Ta buɗe idonta da ya yi ja ya kumbura, da alamun bacci a cikinsa har yanzu, ta ce"Ba zan yi ba!". Ya ce"Ok! Su dai yaranki ai za ki sallame su ko? Yunwa suke ji". A fusace ta ce"Ba zan sallame su ba Sadiq! Ka kira buduruwar taka ta sallame su mana". Ya yi murmushi ya ce"Ok!" Sannan ya fita, ya yi musu wanka ya shirya su, da ya fito da su a falo ya tarar da ita riƙe da kofin shayi, ta taso da sauri ta ce"Ina za ka kai min ƴaƴa?" Cikin ko'inkula ya ce"Inda kika ce na kai su mana". Tana kallo suka fice, ta tashi da sauri ta sako hijjabi ita ma ta fito, a hankali take tafiya, har ta ji mai adaidaita sahu a bayanta, ta shiga ta ce ya dinga tafiya a hankali yana bin bayan Sadiq ɗin, shi kuma sai da ya je titi suka shiga adaidaitar, mai adaidaitar Yusra yana binsu sannu a hankali, zuciyarta sai tafasa take, tana lissafa irin haukan da za ta juyewa wannan yarinyar a yau, huci kawai take yi har suka ƙarasa unguwar su Sadiq, sai dai ganin a ƙofar gidan iyayensa ya tsaya jikinta ya fara sanyi ta gane ba gidan buduruwar zai kai su ba, ta jinjina kai ta ce da mai adaidaita sahun su juya. Suna hanyar komawa, ta ji shigowar saƙo a wayarta, ta duba ta ga shi ne, yake ce mata me yasa ta koma? Ta sani ko auren zumunci zai yi da ƴar'uwar Hajiya? Ta yi ƙwafa ta ajiye wayar. Shi kuwa gidan Hajiyarsa ya kai su, ta tarbe su da fara'arta tana cewa"Yau baƙin safe na yi kenan, ko dai kale kuka zo?" Ya ce"Kamar kuwa kin sani Hajiya, yau koko muke sha'awar sha, muka ce bari mu taho a dama mana". Ta taɓe baki ta ce"Faɗi gaskiya dai, ko tana can gantalin aikin nata ta barku da yunwa". Ya ce"Wallahi Hajiya tana nan, kokon dai muke sha'awa". Ta ce"To mene ne ya hana ka siyan geron idan ba gulma ba? Ko ka siya ta ƙi damawa?" Ya ce"A'a ban siya ba Hajiya, amma tun farko ita ce ta nuna ba ta shan kokon kuma aikinsa wahala ne". "Ku dai kuka sani, ka ƙara aure ka samu mai zaman ibada ka ƙi, kana ta raɓe-raɓe" Ta faɗa tana shiga kitchen, ta kunna gas ta ɗora ruwan koko. Suna zaune yana chart da Ummu Hajiya ta shigo ta kawo musu koko da wainar fulawa, ta zubawa yaran suka fara sha, suna son kokon sosai, duk ranar da ya kawo su gidan sai ta dama musu ko da rana ne, Hajiya ta kalle shi ta ce"Ka yi ka karya ka tafi kasuwarka ka duƙufa a kan waya". Yana ajiye wayar ya ce"Hajiya sabuwar surukarki ce fa, dama ke ce kika ta yi mini fata". Ta taɓe baki ta ce"Yusra tana raye za ka iya yin aure? Mafarki kenan". Ya ce"Wallahi Hajiya da gaske, wata ce a waya muka haɗu, ban ma taɓa ganinta ba, amma gaskiya na yaba da hankalinta". Hajiya ba ta kula shi ba, ya ci gaba da faɗin"A yau nake so dai na je gidansu na ganta, in sha Allah muna gama daidaitawa sai dai ki fara haɗa kayan lefe". "Allah Ya tabbatar" Ta faɗa ba don ta yarda da maganarsa ba. Yana gamawa ya tashi ya tafi ya faɗa mata sai dare zai zo ya ɗauki yaran, kai tsaye shago ya wuce. Wajan ƙarfe goma ya kira Ummu a waya, suna gaisawa ya ce"Ummu a gaskiya na gaji da yadda kike wasa da hankalina, saboda haka ya kamata komai ya zo ƙarshe daga yau, ki kwatanta mini gidanku da daddare zan zo". Gabanta yana ta faɗuwa ta ce"Shi kenan zan nuna maka hotuna...". "Ba na so, face to face nake son ganinki". Ya katse maganar da ta kwaso. Ta ce"Daddyn Afna ina fargabar idan ka gan ni duk soyayyar nan tamu da shaƙuwa ta zama tarihi, ban san da wane ido za ka kalle ni ba a matsayin wacce ta kawo kanta wurinka, na riga na saba da kai ba na fatan abin da zai katse mini buri da farin cikina". Ya yi shiru yana nazari kafin ya ce"Ummu indai kin yarda ina sonki to ki cire duk wani shakku da kike yi a kaina, ko yaya kike ni dai kin yi mini, domin kuwa hali shi ne mutum ba fuska ko halitta ba, kuma halayenki sun yi mini ɗari bisa ɗari". Ta ce"Na yarda da kai, amma ka fara yi mini alƙawarin ba za ka taɓa rabuwa da ni ba, kar ka yi mino hukunci da yadda na zo maka ta bayan fage, yanayi ne ya sa na yi hakan". Ya yi dariya ya ce"Haba Ummu sai ka ce soyayyar waya kanmu farau?" Sosai suka tattauna, ta kwatanta masa gidansu, suka tsaya a kan da daddare zai zo, sannan ta ce za ta yi masa girki ta aiko masa. Wajan sha biyu ta aiko ƙaninta da abincin, cike da zumuɗi ya buɗe yana murmushi, ƙamshi ya daki hancinsa, yana yin cokali ɗaya ya yi shiru yana shakku, wannan sak irin girkin Kursum ne, wanda yake kewarsa a duk ranar da ba ita ce ta yi girkin gidansa ba, amma ta ya hakan zai faru? LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:28 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Ana yin sallar magriba ya tattara kwanukan abincin ya tafi gidan Hajiya, a can ya yi sallar isha'i, suka ci abinci da yaran sannan ya haɗa kansu suka koma gida. Suna shiga suka tarar da Yusra tana ta cika tana batsewa, ta bi kulolin hannunsa da kallo, fuskarsa babu yabo babu fallasa ya ce"Ungo wannan ki wanke mini kafin na fito". Ta karɓa, ya shige ɗaki, ta wanke ta dawo ta ɗakko kulolin abinci ta kawo falon har yanzu babu walwala a fuskarta ta ce da yaran"Ku sakko ku ci abinci". "Mun ƙoshi" Suka haɗa baki wajen faɗa, ta yi ƙwafa, tana jiran fitowarsa. Tsaf ya fito cikin sabuwar shadda, ya zambaɗa uban turare, yana ɗaura agogo a hannunsa yake cewa"Miƙo min kwanukan idan kin wanke". Ta ɗakko su ta miƙo masa ta ce"Na ga kamar fita za ka sake yi?" Ya ce"E". Ta ce"Ga abincinka nan". Ya ce"Abinci sai dai na gobe kuma". Ta ce"Gidan Hajiyar za ka koma?" Ya ce"A'a, me kika gani?" Ta ce"Na ganka da kuloli ne". "Ba nata ba ne" Ya faɗa yana ficewa daga gidan. Ta zauna tana huci mai zafi da tunanin inda zai tafi ya yi kwalliyar nan da daddare, ta kalli Afna ta ce"Afna waɗan nan kulolin na Hajiya ne?" Ta girgiza kai ta ce"Na ga dai ya je da su gidan Hajiya". Ta ja tsaki, ta buɗe abincin ta zuba, sai dai ta kasa ko cokali ɗaya sai juya shi take tana tunani da fargaba sosai. Tsaf Sadiq ya bi kwatancen Ummu, ya je har ƙofar gidan da ta ce nan ne gidansu, sannan ya tsaya ya kirata a waya, tana ɗagawa ya faɗa mata yana ƙofar gida, babu jimawa ta fito kanta a ƙasa, ta yi masa sallama, ya amsa yana murmushi cike da zumuɗin ganinta, "Ai ɗagowa za ki yi ki kalle ni, mu ga juna kuma ki buɗe baki yau na ji duk kalamanki na cikin waya a zahiri". Murmushi take yi, amma zuciyarta tana bugawa, sai dai ranar wanka ba a ɓoyon cibi, komai ya zo ƙarshe dama ita jarabawa ɗayan biyu ne ko dai nasara ko akasinta, don haka ta ɗago ta buɗe mayafinta sosai, ta danna wayarta ta kawo haske dalilin da ya bayyana fuskarta tarr ta dake zuciyarta ta ƙi kallonsa tana cewa"Ina fatan har yanzu alƙawarinmu yana nan, baban Afna ka ce za ka so ni a duk yadda nake". Shi kuwa Sadiq mugun mamaki ne ya daskarar da tunaninsa, ya kasa yarda da gaske Kursum ƴar aikin gidansa yake kallo tsaye a gabansa a matsayin sabuwar masoyiyarsa Ummu, wacce yake jin za ta iya taka duk wata rawa da Yusra take takawa na matsayin matarsa. "Kursum!" Ya kira sunanta da alamun mamaki. "Na'am". Ta amsa tana yi masa murmushi. Sai ya yi murmushi ya ce"Nawa Yusra ta biya ki ki yi mini wannan jarabawar?" Ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Haba dai, a zamanin nan kake tunanin akwai macen da za ta yi wannan wasan kurar da mijinta kuma miji ma kamar ka?" Ya ce"Ki faɗa mini gaskiya Kursum, Yusra ce ta shirya komai ko? Yanzu kin sanar mata komai na tarkonta ya ɗanu kenan ta gane mijinta zai iya rayuwa da wata ba ita ba ko? Good!" Ya ajiye mata kulolinta zai tafi, ta yi saurin zuwa gabansa ta tsaya tana girgiza kai ta ce"A'a! Baban Afna ka fahimce ni, sam Yusra ba ta da masaniya a kan soyayyarmu, na shigar da kaina ne da raɗin kaina, duk da na san za ka ga zaƙewata da yawa, ina ƴar aikin gida na ce ina son mai gida, wannan tsaurin idon zuciyata ne, kuma ka san shi so makaho ne, ba ya ganin inda zai je, ba ya duba cancanta, ni dai na san ba mu dace da juna ba, ka wuce ajina ta kowane fanni, shi yasa ma na biyo ta haka na kasa faɗa maka ta yadda ya kamata, don Allah ka yi haƙuri, a yanzu kana da damar zaɓawa kanka hukuncin da za ka yi mini, kuma ya zama dole na karɓa tun da ni ce na jawo komai, amma ka sani soyayyar da na nuna maka ba wasan kwaikwayo ba ce, saboda haka ka yi wa zuciyata adalci wurin yi mini hukuncin". Tun da ta fara magana yake kallon yadda take hawaye tamkar an kunna famfo, kai ya girgiza yana huci, bai taɓa zaton ranar da ya yi ta jira ta haɗuwa da masoyiyarsa za ta zo masa a haka ba, bai taɓa zaton ya san yarinyar da suke soyayya ba, lokuta da dama ya sha jin kamar ya san muryarta a wani a wajen, amma sai ya kasa tuna inda yake jin irinta, tunani kawai yake yi me yasa Kursum za ta yi masa haka indai ba dama can saboda haka ta zo gidansa ba? Shassheƙar kukanta ya sa shi cije baki ya ce"Shi kenan, ki je gida, idan na yi tunani zan neme ki". Daga haka ya tafi, ya barta da share hawaye, gida ta shige ta je ta kwanta a katifarta, sabon ruwan hawaye ya ɓalle mata, sosai take mutuwar son Sadiq, a yadda ta saba da shi ba ta jin za ta iya barin shi ta sauƙi, saboda haka yanzu za ta fara yaƙin ƙwatarsa a hannun Yusra ta ƙarfi. A sanyaye ya koma gida tunanin barkatai a ƙwaƙwalwarsa, a falo a tarar da Yusra tana kallo, da alama yaran sun yi bacci, kallo ɗaya ya yi mata zai wuce ta tashi ta sha gabansa ta ce"Wai kana nufin wannan abincin haka zai kwana, na dafa a banza kenan?" Ya ce"Ai ba ni na ce ki dafa ba". Ta ce"Amma na ga ko ka ci a gidan Hajiya kana cin na gidan ko yaya ne, sannan ina ka je? Kuma waɗan nan kulolin ina ka kai su? Na wace?" "Ƙila fushi na yi saboda da safe kin nuna ban isa ki dafa min ba, shi yasa yau na ƙi cin komai naki" Ya faɗa yana raɓeta zai wuce. Ta sake tare shi ta ce"Ai ba ka ba ni sauran amsoshina ba, waɗan nan kulolin..." "Na buduruwata ne, daga can nake na mayar mata, jikinta ya ba ta ban ci abincin rana ba, shi yasa ta dafo min". Ya faɗa yana wucewa, a wannan karon ba ta tare shi ba, saboda takaicin maganganunsa sun kashe mata jiki, duk da ba ta yi mamaki ba, amma sosai abun ya baƙanta mata, ta koma ta zauna, ta riƙe baki tana tunanin mafita. Shi kuma kaya ya canza ya kwanta rigingine yana jin wani irin yanayi mara misaltuwa, shi ba baƙinciki ba, kuma ba farinciki ba, abu ɗaya da ya sani shi ne yana son Ummu, yana son halayenta, sannan yana son halin Kursum wanda ya sani, yana son irin kwalliyarta da girkinta, sai dai ta ya zai shigar da Kursum ƴar aikin gidansa cikin Ummu masoyiyarsa su haɗu su bada Ummu Kursum? Ta ya zai kalli Yusra ya faɗa mata ƴar aikin da ta ɗakko da hannunta ta yi masa kwantan ɓauna ta sace zuciyarsa? Soyayyarsu halattacciya ce wacce za ka yi wa aurensu kallon mai tsarki kuwa? A idanuwan mutane yake nufi, da kuma wurin Yusra shugaban ƴan kishi. Shigowar saƙo wayarsa ya katse masa tunani, ya janyota ya duba, ita ɗin ce kamar yadda yake zato, bayan sallama ta ce 'Don Allah kada ka tsawaita lokacin tunanin, saboda duk sakan ɗaya bugun zuciyata ƙaruwa yake da fargabar karɓar hukuncin da taka zuciyar za ta zartar wa soyayyarmu, ina son ka Sadiq'. Ya sauke ajiyar zuciya yana ajiye wayar. GIDAN ALI A hankali Maryam ta taso, saboda kanta da yake sarawa, na tsananin ciwon da tunani ya haddasa mata, ta buɗe ƙofar a tunaninta maƙota ne, ta yi turus ganin Ali yana sakar mata murmushi, da sauri ta yi yunƙurin mayar da ƙofar ta rufe, cikin zafin nama ya tura ƙofar ya shiga, yana cewa"Haba Maryam mene ne haka?" Hawaye suka zubo mata, ta shige ɗaki ta zauna ta fashe da kuka, ya shigo da kayansa tsaf, sannan ya ƙarasa inda take cikin mamaki da firgici, ya riƙo ta, ta fizge cikin hargagi take cewa"Kar ka sake taɓa ni!". "Innalillahi!" Ya faɗa zuciyarsa tana bugu, sannan ya koma gefe ya zauna, ya yi shiru yana nazarin dalilin da zai saka ta yi masa haka daga dawowarsa. Can dai ya sake matsowa da sanyin murya ya ce"Yanzu Maryam wannan ita ce tarbar da ya kamata ki yi wa mijinki wanda ya zaɓi nesa da gida har na tsawon kwana bakwai yana can yana aikin ƙarfi cikin zafin rana, saboda rufin asirinki?" A fusace ta ce"Saboda rufin asirinka dai! Ali ina ka je tsawon kwanakin nan!?" Gabansa ya faɗi, ya haɗe gira ya ce"Maryam kanki ɗaya kuwa? Ni kike tambaya ina na je, bayan kin fi kowa sani?" Ta ce"Kaina ɗaya! Wace ce Hajiya Zuwaira, da ka turo ta ta faɗa mini kana garin nan ƙarya ka yi mini na cewar ka tafi Enugu?" Ƙirjinsa ya buga da ƙarfi, ya haɗiyi wani yawu mai tauri na fargaba ya ce"Ban gane ba, wace ce kuma Hajiya Zuwaira? Ni ban taɓa jin sunan nan ba". Maryam ta yi murmushin takaici tana kuma hawaye ta ce"Na yi bincike a kan komai, ashe kana garin nan babu inda ka je, abokan naka da ka ce kun tafi tare duk na bi gidajensu matansu sun tabbatar mini babu inda suka je, ina ka je Ali, wannan ƙamshin da kake yi iri ɗaya sak da na Hajiyar da ka turo mini". Ali fa ya gane ya gama kamuwa tass, amma ya ƙi miƙa wuya, ya tashi a fusace ya ce"Shi kenan Maryam tun da zargina kike yi ki je ki yi ta yi, ki ci gaba da ɗaukar zugar mutane babu komai, laifina ne da tun farko na bar ki kike kafa mini dokoki ina bi, alhalin ke ce a ƙasana, ban hana ki ci da sha ba, na yi miki sutura, na bar ki kina sana'ar da kullum kike cika min gida da mata, shi ne za su kashe miki aure kenan saboda ke shashasha ce za ki hau gadar kwali ta rufta da ke, ki je ki yi ta yi!". Ta yi wata dariya ta ce"Tabbas ni shashasha ce da na yarda da kai, kuma na yarda da duk tsarin da ka yi mini, dama tabarmar kunya da hauka ake naɗeta, babu komai Ali ka je ka yi, duniya ce, idan har kana cutata a zamanmu na barka da fitowa da faɗuwar rana". Daga haka ta fice daga ɗakin. Ali ya dafe kansa yana jin ƙuna a zuciyarsa, ya ma rasa ta ina zai fara, wane ne ya yi masa wannan ɗanyen aikin haka? Sunan Hajiya Zuwaira ya dawo masa, shi fa sam bai san ma sunan Hajiyarsa ba, ya ɗakko waya da sauri, ya kira ta, tana ɗagawa ya ce"Hajiya don Allah ya sunanki?" Ta yi dariya ta cikin wayar ta ce"Ikon Allah! Sai yanzu kake tambayar sunana?" Shigowar Maryam ta katse maganar da yake shirin yi, ta ce"Idan ta faɗa maka sunan nata, sai ka fito ka yi wanka, ban yi girki ba me zan dafa maka?" Ya kasa cewa komai, ya ajiye wayar, yana ɗan haɗe fuskarsa, zuciyarsa kuwa fal take da nadama. Tana girki tana share hawaye, har ta gama dafa macaroni ta kawo ta ajiye, yana zaune a yadda ta bar shi, ta zuba a plate ta ci, ta sha magani ta tafi ta kwanta, tana ƙarfafar zuciyarta, don za ta ajiye wannan a matsayin sirri shiyasa ma ba ta bari kowa ya san wani abu a kai ba, ta je dai gidansu ta ji nan ma yadda ya tsara mata haka ya tsara musu, sai kuma abokansa da ta gano suna gari, za ta barsa da halinsa, amma duk ranar da wannan karuwar ta yi gangancin dawo mata gida za ta gane Allah ɗaya ne. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 ALI Sai wajen ƙarfe tara ya tashi ya shiga ɗakin jikinsa a sanyaye, tana kwance idonta a buɗe, ya janyo ledar kayan kusa da gadon da take ya ce"Maryam ga wannan kayan". Ba ta ce komai ba, ta bi shi da kallo, ya ce"Ki yi haƙuri don Allah, shi ne kawai abin da zan iya ce miki, tun da an riga an zuga ki an ɓata ni a idonki, komai na ce miki yanzu ba za ki yarda, amma lokaci shi zai faɗa miki wane ne mijinki da kuma matsayinki a wurina". Ta ce"Ali ta ya zan yarda da kai bayan ga ƙamshin turaren matar nan a tare da kai? Ka ce min tare da abokanka kuka tafi amma na gano cikinsu kai ɗaya ne kawai ba ka nan". Ya ce"Wallahi Maryam Enugu na je na yi aiki, ban san komai ba a kan matar nan, ko wayar da kika ji ina yi wata mata ce ta dame ni da kira wallahi, wai ta san ni, ni ma na santa, shi ne nake tambayarta ya sunanta, amma wallahi Maryam ba abin da kike zato ba ne". "Hmm!" Kawai ta ce, tana ji a ranta za ta ga ƙarshen ƙaryarsa. Ya buɗe ledar ya fara fito da kayan ciki, ya ajiye mata nata ya ce na sallah ne ya siya mata, shi kuma nashi gwando ne giredi ya ga suna araha a can shi ne ya siya, ya miƙo mata kayan ciye-ciyen ya ce"Ga wannan su ma a tasha na siya". Ta ce"Ka tabbatar ba wannan yarinyar da take sonka ce ta sake aiko maka ba?" Ya ce"Haba Maryam, wallahi a tasha na siya, sauri nake ta yi ma ina zumuɗin ganinki shi yasa ban tsaya siya miki kwakwa da dabino ba, amma gobe za ki ci ki mori". Ganin ta tsaya tana kallonsa sai duk ya tsargu, ya ce"Haba Love don Allah ki saki jikinki mana, ko har yanzu ba ki yarda da ni ba?" Ta ce"Gani na yi duk ka kashe kuɗin aikin da ka samu, shi ne jikina ya yi sanyi". Ya ce"Laa! Kar ki wani damu, ai sai da na je na ga ashe dubu ashirin ne kullum, shi yasa na yi siyayyar nan, akwai sauran kuɗin ai, kuma tun da ga shi har da kayan abinci na siya kin ga ai na rage ko?" Ta gyaɗa masa kai alamar haka ne, ya ce"Don Allah ki saki jikinki, sakko ki ci ko dambun nama mana". Ta ce"Zan ci, sai gobe". Ya ce"To bari na ci macaronin, wallahi da na kasa ci saboda ganin yadda kike zargina, abun ya dame ni, amma yanzu har na ji daɗi". Ta ce"Babu komai, ciki da gaskiya ai wuƙa ba ta huda shi". Ya koma falo ya ci macaronin kaɗan, ya dawo ya ce"To ki duba kayan mana, ki ɗibarwa ƴan gidanmu zan kai musu yanzu". Ta sakko ta ɗibar mata, ya fita ita kuma ta koma ta kwanta. Yana fita ya kira Hajiya a waya ta ɗaga ta ce"Aliyyuna shi kenan fa ka koma gida sai sanda na ji ka, Maryam za ta kanainaye ka ko?" Ya ce"A haba Hajiya wannan da ne, yanzu dole na fara tsawatar mata ai". Ta yi dariya ta ce"Allah Ya sa da gaske". Ya ce"Hajiya ɗazu muna magana, wai sunanki Zuwaira dama?" Ta ce"A'a mene ya faru? Ni Aisha sunana". Ya ce"Tsakani da Allah ba ki je gidana ba cikin satin nan? Maryam ta faɗa mini wata Hajiya ta je mata ta faɗa mata mijinta yana Enugu..." Ta katse shi da faɗin"Haba Aliyyu kuma ban da ragon tunani irin naka ta ya zan toshewa kaina ƙofar farinciki? Ka san irinku masu mu'amula da mata, wata a cikinsu dole ta yi kishinka, wata kuma ƙila kun samu saɓani sai ta nemi ruguza farincikin gidanka, amma ni kam ba ni ba ce, akan me zan je na yi magana da yarinya ƴar cikina?" Ali ya ce"To shi kenan Hajiya, zan yi bincike". Daga haka suka yi sallama, yana ta tunanin idan ba ita ba ce wace ce? Ya je gidansu suna ta yi masa sannu da hanya, ya ba su tsaraba ya bawa babarsa dubu goma ya koma gida, Maryam har ta yi bacci, ya kwanta shi ma bacci ya kwashe shi cike da kewar gidan Hajiya. GIDAN SADIQ Washegari da safe Yusra ruwan shayi kawai ta dafa musu ta ɗumama abincin jiya, ko wanka ba ta yi wa yaran ba suka tafi makaranta saboda ta makara da safe, har lokacin ma bacci ne fal idonta, bayan sun tafi makaranta ita ma ta tafi asibiti. Babu jimawa Kursum ta zo, shagon Sadiq ta wuce kamar yadda ta saba don karɓar mukulli, sai dai yau ta tsinci kanta da kunyar haɗuwa da shi, saɓanin baya da take shauki da zumuɗin ganinsa a kullum, babu kowa a shagon ta ƙarasa da sallama tana sunkuyar da kai ta gaishe shi, ya amsa kamar komai bai faru ba, ya miƙo mata mukullin ta ɗauka ta tafi, a zuciyarta tana fargaba sosai na kar dai Sadiq ya yanke hukuncin rabuwa da ita ne. Sha biyu ta gama komai har girki, ta ɗauki nashi ta tafi kai masa, wannan karon ma bai ce komai ba har ta ajiye ta tafi, jikinta a sanyaye ta shirya yaran da suke ta yi mata surutu, wanda yau hankalinta duka ba ya kansu, yara sun tafi islamiyya tana shirin wucewa gida Yusra ta kira ta a waya, ta ce ta yi mata tuwo kafin ta tafi. Kafin ta gama tuwon ta dawo, har yanzu jikinta a sake yake, kana kallonta ka san tana cikin damuwa, don tana shiga asibiti Sumayya ta tare ta da tambayar damuwarta, ta ce ta ga yanayinta babu kyaun gani, murmushi kawai ta yi ta ce mata"Kaina ne yake ciwo, amma na sha magani". Sumayya ta yi murmushi bayan ta wuce don jiya Kursum ta sanar da ita komai na fashewar ƙwai, ta san watan fara ɗanɗana maɗacin Yusra ya tsaya ƙyam, saboda haka dole ta bibiyeta tamkar ɗalibi da karatu don ta dinga jin matsayarta akan Sadiq don idan ta samu mafita ita kuma ta nemo hanyar da za su rufe ita da Kursum har zuwa lokacin da auren nan zai tabbata, shiyasa da ta ganta zaune ba ta aikin komai ta sake zuwa tana nuna damuwa da yanayinta ta ce"Ƙawata yaushe kika fara ɓoye mini sirrinki? Ba iya ciwon kai ne damuwarki ba, ki sanar da ni, ƙila ina da shawarar da zan iya ba ki". Yusra ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Hakane ba na ɓoye miki komai nawa, amma wannan family issue ne". Sumayya ta ce"Haba Yusra, ni da ke kuma ai an zama ɗaya, har akwai abin da za ki ɓoye mini na familynki?" Yusra ta yi murmushi ta ce"Sorry, idan ina neman shawara zan same ki". Daga haka ta tashi ta bar wurin, saboda sosai take son kaɗaici, sam ba za ta iya faɗa mata da gaske Sadiq zai yi mata kishiya ba, saboda a ganinta wannan wani babban abun kunya ne, duk da ta sani shi ma ya sani, babu zama da kishiya a tsarin rayuwarta har abada. "Anti sannu da zuwa, ya aikin?" Kursum ta faɗa bayan shigowar Yusra. Yusra tana zama ta ce"Yawwa Kursum, kema sannu da aiki". Ta yi murmushi ta je ta zubo mata abinci da ruwa ta kawo mata, tana cewa"Bari na kwashe tuwon, har na gama miyar". Yusra tana janyo abincin ta ce"Na gode Kursum". Tana gama komai ta fito za ta tafi Yusra ta ce"Kursum gobe ina so ki yi mini cake na kwano biyu". Ta ce"To Anti babu matsala Allah Ya kaimu". Yusra ta ce"Amin, gaskiya ina godiya sosai, wallahi na yi dace, ba ki da gandar yin aikin komai, gyaran da kike yi ko ni iyaka kenan". Kursum ta yi murmushi ta ce"Haba babu komai Anti, wannan ai yi wa kai ne". "Yi wa kai kuma Kursum?" Yusra ta faɗa da ɗan mamaki. Kursum ta ce"To Anti shi ɗa ai na kowa ne, ni wallahi yadda yaran nan suka shiga raina ina jinsu kamar ƴaƴana babu abin da ba zan iya yi a gidan nan ba, kuma idan kika yi duba da fita aikin nan naki kina yi ne don taimakon al'uma musamman mata, ai don wata mace ta zo gidanki ta yi miki hidima ba ta faɗi ba, kuma ga aiki har da na kwana ga kula da mai gida kin ga ai kin cancanci a taimaka miki, shi yasa ni kam zan yi miki wannan sadaukarwar na kula miki da gidanki". Yusra ta yi murmushi ta ce"Na gode sosai Kursum, gaskiya zan yi kewarki ranar da kika samu mijin aure". Kursum ta ce"Ai muna tare ma". Yusra ta yi dariya don ba ta fahimci komai ba, suka yi sallama Kursum ta tafi. GIDAN HARUNA Sosai laulayi ya sake kwantar da Halima, tamkar gidan ne cikin ba ya so, muguwar kasala ce take damunta, da ta ci abinci sai amai, har yanzu Zainab ce take yin abincin siyarwa, sai ta raba ribar biyu ta bawa Halima rabi, haka girkinta da sauran aiki duka ita ce take yi mata, daga ranar Haruna bai sake yarda sun haɗu da Zainab ba, sai dai su yi ta chart ɗin banza a waya, duk da sosai yake kewarta amma yana jin tsoro, ya lura ita sam ba ta saduda ba, ba ta da tsoro sam, a lokuta da mata shi yake ƙi idan ta ce masa ga dabara. Satin su biyu a haka, watarana dai Zainab ta matsa masa da son su haɗu, ta ce ya siyo maganin bacci za ta bawa Halima da Baaba su sha su baje, su kuma su samu sakewa, sai ya yarda da wannan shawarar, ya siyo magani ta tare shi a zaure ta karɓa, bayan isha'i ne amma haka ta kunna wuta ta dama kunu, ta zuba magani a na Halima da na Baaba, tana miƙawa Baaba ta fara sha don dama har ta fi Zainab son kunun, ta zabga maganin na Halima ya fi yawa, ta juya tsaf ta zabga suga ta yi sallama da fara'arta ta ce"Halima ga kunun alkama". Halima ta tashi zaune tana murmushi ta ce"Zainab kunun naki har da daddare? To na gode kuwa". Haruna yana zaune yana danna waya, yana kallonsu ta gefen ido, Zainab ta ajiye mata kunu ta fita bayan ta faki idon Halima ta kashe masa ido, shi kuma ya yi murmushi. "Ga kunu ko za ka sha" Halima ta faɗa tana miƙa masa. Ya yi saurin girgiza kai ya ce"A'a kunanun nan, na gode". Ya tashi ya fice waje. Halima tana kai kofin kunun bakinta, ta ji zuciyarta ta fara tashi, ta yi saurin saukewa, ta mayar ta rufe, ta ɗakko farar ƙasa ta fara tsotsa don ta dakatar mata da amai, ta koma ɗaki ta kwanta. Sanda Haruna ya dawo sha ɗaya ta yi, a lissafinsu Halima da Baaba sun yi nisa a duniyar bacci, saboda haka ko da ya dawo ya tarar da Halima tana bacci jikinsa yana rawa ya kira wayar Zainab, ta fito don dama jiran kiran nasa kawai take, ta shigo ɗakin nasu cike da shauƙi tana cewa"Kai da na ce ka dawo tun ƙarfe tara mu fara kafin maganin ya sake su?" Ya ce"Ke yi a hakanli fa kar ta farka". Ta ce"Haba ni Baaba ɓa nake ji, amma Halima wannan zabga mata ai ko da asuba sai ta yi da gaske za ta iya yin sallah". Halima dake kwance ƙirjinta ya buga da ƙarfi, don tun motsin shigowar Haruna da ta ji ta farka, so take ma ta sakko ta je banɗaki, sai kuma ta ji ya rufo ƙofa, muryar mace da ta ji ne kuma ya firgitata, sauraron kalamansu da gane muryar Zainab saura kaɗan ya sa ta ƙware da yawun bakinta, ta yi luf a gado zuciyarta tana ta tsallen baɗake tamkar za ta fasa ƙirjij ta fito, tun tana jin ƙus-ƙus ɗinsu har ta ji shiru, kafin ta fara jin alamun sun yi nisa a wata duniyar, innalillahi wa inna ilaihi raji'un ta dinga maimaitawa a zuciyarta, jin kunnuwanta ba za su iya ɗaukar sautin mijinta da yake ta zuba sambatun fitar hayyaci wanda ko ita da take matarsa ba ya yi mata shi ba, ya sa ta sakkowa daga gadon tsam, ta kunna fitilar wayarta ta fito falon, har lokacin ba su ji motsinta ba, sai da ta haske su tare da fashewa da kuka cike da nadamar fitowa don mummunan ganin da ta yi saura kaɗan ya kayar da ita, a zabure duka suka miƙe, zuciyoyinsu na bugu, Zainab ta saka kayanta ta fice a sanyaye, ta koma ɗaki ta kwanta ta yi luf. Shi ma kayan ya saka ya zauna a falo ya yi shiru ya ma rasa me ya kamata ya yi. Ita kuwa Halima durƙushewa ta yi a cikin ɗaki, ta kifa kanta a gado kukan ma sai ya tsaya cak, sai wani malolon abu da ya cika mata maƙoshi yake barazanar toshe mata numfashi, ajiyar zuciya take ta saukewa da sauri-sauri, inda ta san wannan halin za ta shiga bayan ganewa idanunta wannan mummunan lamarin, da ba ta fito ba, tunani kawai take yi na dama da gaske akwai masu irin wannan rayuwar? Har cikin ɗakinta kuma tana nan labule ne kawai ya raba su amma mijinta saboda shahara a iskanci ya iya kawo mata mace? A yadda ta fahimta ma ba ya suka fara yi ba, har tsawon wane lokaci suka ɗauka suna aikata hakan, ba tare da saninta ba, Baaba ma me take yi da ba ta fahimta ba? Ta saki kuka mara sauti tana damƙe zanin gado, a haka suka kwana ita a durƙushe, shi kuma a falo. Da asuba ta fito sallah ta same shi kwance a kujera yana baccinsa, ƙarar buɗe ƙofa ne ya farkar da shi, don dama baccin rabi da rabi ne, ya farka a firgice ya ce"Zainab!". Halima ta juyo ta ce"Na turo maka ita ne?" Ba ta jira cewarsa ba ta fice, ta yo alwala ta dawo ta tada sallah, shi ma sum-sum ya tashi ya yi alwalar ya fice daga gidan, har gari ya fara haske bai dawo ba, tana jin motsin Zainab ta fito ta kunna wuta, ta buɗe labule kaɗan ta leƙa ta kalle ta, ta saki hawaye ya ɓalle mata, tana sharewa wasu suna zubowa, ta ma rasa matakin da ya kamata ta ɗauka, ta rasa wa za ta fara faɗawa kanta ya kulle don ba ta taɓa zaton mijinta yana neman mata ba, haka ma Zainab ɗin kallon yarinyar kirki take yi mata, ta kwantar da kanta a kujera ta lumshe ido tana karanto Allah humma la sahla, har zuwa lokacin da Zainab ta yi sallama a ɗakin nata, kafin ma ta amsa ta shigo, kanta a ƙasa ta ce"Ina kwana Halima". Sai Halima ta kalle ta ba tare da ta amsa mata ba, don ba ta yi zaton Zainab za ta iya sake haɗa ido da ita ba, ita kuwa Zainab kwano da kofi ta miƙa mata tana cewa"Ki karya Halima, sai ki sake kwanciya wataƙila jiya ba ki samu bacci ba". Daga haka ta juya ta fice, Halima ta bi ta da kallo kamar sakarya. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN HARUNA Tana zaune kamar an dasa ta har Zainab ta fara hada-hadar dafa abincin siyarwa na rana, har lokacin Haruna bai dawo ba, sai a sannan ne kuma Baaba ta fito tsakar gida tana kiran sunan Halima, jin wasu hawaye sun zubo mata sai ta amsa ta kasa fitowa, a ƙofar ɗakin ta tsaya don ba ta fiya shiga ba ta ce"Halima yau ban ji ki ba ko jikin ne?" Halima ta daure ta tsayar da hawayen ta fito tana cewa"Baaba ina kwana?" Baaba ta ce"Lafiya lau, na ce ba ki fito ba bari na keƙo ki, wallahi jiya wani bacci na yi mai nauyin tsiya, har yanzu gaɓoɓina a sake baccin bai ishe ni ba". Halima ta kalli Zainab, da take tsince shinkafa, suka haɗa ido ta mai da kanta kan farantin, Halima ta ce"Ayya Baaba ai da kin koma kin kwanta, ni ma yau jikin nawa ne babu daɗi shi yasa ban fito ba". Baaba ta ce"To ma sha Allah tun da ƙalau kike". Halima ta ce"Lafiyata lau, ki je ki yi baccinki, amma ki daina shan kunu ko abu mai ruwa da daddare ƙila kunun ne ya kashe miki jiki, kina da ƴa irin Zainab a gabanki bacci da nauyi bai kama ki ba Baaba, don ma dai Zainab akwai nutsuwa". Baaba ta ce"Ai kuwa dai ina ga rashin sabo da shan kunun daren ne kam, zan daina sha don wannan bacci na jiya sai a yashe gidan tsaf a watsa ni a mota a kai jeji a zubar duk ban ji ba". Halima ta yi dariya ta ce"Ni ma bari na kwanta, kasala ta dame ni". Daga haka ta shige ɗaki, ta kwanta, sai dai ta kasa baccin duk da tana ji, amma da ta tuna wannan mummunan ganin da ta yi sai kanta ya fara juyawa zuciyarta ta dinga azalzalarta, baƙinciki ya hana ta baccin, tana nan zaune Zainab ta shigo ta ajiye mata kular abincin da ta gama dafawa, ta fita, ta kalli abincin don wainar safe ma da ta ajiye tana nan a wurin ba ta taɓa ba, mamakin ƙarfin halin Zainab kawai take yi, sai yamma lis da ta ji yunwa ta dame ta sannan ta zuba shinkafa da waken kaɗan ta ci, ta sha ruwa, Zainab ta shigo kamar yadda ta saba tana sosa kai ta ce"Halima me za a dafa muku da daddare?" Halima ta ɗaga kai ta kalle ta, ta haɗiyi wani yawu ta ce"Ki tambaye shi". Sum-sum Zainab ta fice, ta tafi harkarta. Sai isha'i Haruna ya dawo, lokacin tana zaune a sallaya, ya shigo da sallama a sanyaye da ledarsa, ta amsa tana kallon shi, ya ƙi kallonta ya miƙa mata ledar ya ce"Ga wannan". Ta buɗe ta ga kaza ce da biredi ga yougurt mai sanyi, ta yi murmushin takaici ta ce"Ni kuma ai ban cancanci wannan ba, zai fi kyau da wacce ka ɗauka a matsayin mace ba ni ba". Yana cire kaya ya ce"Ki yi haƙuri Halima, ni kaina ban san mene ne ya hau kaina ba, amma mu bar hakan a matsayin ƙaddara kawai, ba zai sake faruwa ba in sha Allah!". Halima ta ce"Haruna ka dinga tunawa gobe kai uba ne, idan haka ta faru da ƴarka ya za ka ji? Kai yayan wasu ne, za ka so haka ta faru da ƙannenka? Haruna abun ya kai har cikin ɗakina, ina ciki kuna falo labule ne kaɗai ya yi mana katanga? Wace irin matsuwa kuka yi da juna kuma tun yaushe kuka fara cin amanarmu ni da Baaba? Haruna me na yi maka, ko ba na ba ka haƙƙinka ne?" Ya ce"Na faɗa miki ƙaddara ce kawai, kuma wa man ƙadarallahu haƙƙa ƙadrihi..." A fusace ta ɗaga hannu ta ce"Don Allah Ya isa haka kar ka yi mana saɓo, ni yanzu alfarma ɗaya nake nema a wajenka, ka ba ni takardar sallamata kawai domin ban ga amfanin aurenmu ba, saboda daga jiya zuwa yau kaf mutuncinka ya gama tsiyayewa a idona, rabuwa da kai shi ne maslaha idan ba haka ba, wani irin zama za mu fara yi wanda ni ce zan dinga cutuwa, wani auren zai iya kai mace wuta, saboda haka ka sallame ni shi ne kaɗai adalcin da za ka yi mini, kuma shi zai zama rufin asirinku, ya kuma ba ku damar auren junanku ku yi rayuwar halal ba ta haram ɗin da kuke ciki ba". Bai ce komai ba ya yi hanyar ficewa daga ɗakin, ta ruƙo hannunsa ta ce"Haruna ka sake ni tun ban tona maka asiri ba!". Da ɗan ƙarfi ta faɗa, hakan ya razana Zainab dake laɓe a ƙofar ɗaki tama sauraronsu, ta shige ɗakinsu ta kwanta tana fatan Allah Ya sa dai ya yarda ya sake ta ɗin, duk da ba za ta iya auren Haruna ba, amma idan ba shi da aure sai ta fi tatsarsa sosai. Haruna ya fizge ya ce"Halima ba zan sake ki ba!". Ya fice daga ɗakin. Ta zauna ta fashe da kuka, kafin ta tashi ta fara haɗa kayanta a jaka, ta gama tass tana shirin fita ya fito daga wanka, ya yi saurin zura jallabiya a jikinsa ya riƙe ta yana cewa"Halima ina za ki je? Yanzu ba za ki yi haƙuri ki rufa mini asiri ba? Wannan ne fa na farko ki daure ki ba ni dama ta biyu ki gani, yanzu ke idan na sakeki kika yi wani auren kin san me za ki tarar a can, kuma wa za ki aure?" "Me kyakkyawar zuciya zan aura kuma alkhairi zan tarar in sha Allah!" Ta faɗa da ƙarfi tana fizge hannunta daga ruƙon da ya yi mata. Ya ce"Shi kenan Halima, ki je inda zuciyarki ta fi karkata, amma ni dai ban sakeki ba, kuma ba zan sakeki ba, sai dai ki zama mai riƙe sirrin aure, don ƙila ni ɗin dai Allah Ya zaɓa miki mu zauna har ƙarshen rayuwa, yau idan kika tona mini asiri saboda kuskuren rana ɗaya, kika ja mutane suna kallona a baƙin mutum ba har abada ina ranar irin haka?" Ta ce"In sha Allah ba zan rayu da kai har abada ba!" Daga haka ta fice daga ɗakin Ya ɗakko ledar da ya shigo da ita yana cewa"To mu je na raka ki". "Ni ban nemeka ba!" Ta faɗa a fusace. Baaba da take alwala ta ce"A Halima fita za ku yi?" Ya yi saurin cewa "E Baaba, jikin ne ya motsa, ta ce kuma ta fi jin daɗin zaman gidan nasu". Halima ta fice ba tare da ta cewa Baaba komai ba, shi kuma ya bi ta da sauri, Baaba ta bi su da kallon mamaki. Tana shiga adaidaita sahu shi ma ya shige, suka ƙarasa ƙofar gidan, kafin ya sallami mai adaidaita har ta shige ciki, shi ma ya yi sallama ya shiga, da yake Umma shafa'i da wutri take yi, duk sai suka zauna, tana idarwa suka gaisa tana tambayar lafiya? Haruna ya ce"Dama jikin ne dai, shi ne ta ce ta fi son zaman nan ɗin, sai na ce to ta zo ta huta babu damuwa". Umma ta kalli Halima ta ce"Haba Halima, sai ka ce ƙaramar yarinya? Ko da haihuwar farko ce ai ke ba yarinya ba ce da za ki zaɓi zaman gida ki bar mijinki!". Hawaye suka zubo mata, ta tashi ta shige uwar ɗaki ta kwanta tana kuka mara sauti. Haruna ya ce"A babu komai fa Umma, ai larura ce, mu yi haƙuri duka" Ya ajiye ledar ya yi mata sallama ya tafi, zuciyarsa cike da fargabar kar ta tona asirin nan. Saurin share hawayenta ta yi da ta ji shigowar Umma, ta zauna a gefen gadon ta ce"Halima bai kamata ki ta dawowa gida saboda laulayi ba". Halima ta ce"Wallahi Umma gidan babu daɗi, ba na iya bacci". Umma ta ce"Sai haƙuri ai dama, Allah dai ya raba lafiya kin ci abinci?" Ta girgiza mata kai, Umma ta fita ta zubo mata dambu ta kawo mata ruwa, ta ci a ƙoshi, ta yi wanka ta kwanta bacci mai nauyi ya ɗauke ta. Bayan ta yi sallar asuba ma baccin ta koma, ta yi sosai ta wartsake, ta tashi ta yi wanka, sanan ta Umma ta haɗa mata shayi da biredin da Haruna ya siyo suka ci kaza da yougurt suna fira jifa-jifa, idan tunanin abin da ya faru ya zo kanta sai ta yi saurin kaudawa, haka ta wuni tana jin gara zaman gidansu a kan na mijinta. GIDAN ALI Da safe ta tashi babu yabo babu fallasa, suka karya ya tafi wurin aikinsa, ta ɗakko tsarabar ta duba ta ɗauki nata, ta bar masa nashi, a zuciyarta tana fatan Allah Ya sa zatonta ba gaskiya ne, idan kuma gaskiya ne Allah Ya shirye shi Ya ganar da shi hanya madaidaiciya, da daddare ana sallar isha'i ya dawo, tun kafin ya shigo ya kashe wayarsa shi yasa suka yi ra firarsu hankali kwance, a haka dai har ta saki jikinta suka koma kamar yadda suke da, ta samu nutsuwa sosai ganin ba ya ma firar daren da wuri yake dawowa su zauna, shi kuwa a nasa ɓangaren sosai hakan yake azabtar da shi, yana yi ne kawai saboda ta saki jikinta ta sake yarda da shi sosai, amma ya yi kewar Hajiya har tsawon sati ɗaya sai dai su yi waya idan yana waje, duk wani chart kuma sai Maryam ta yi bacci yake yinsa a falo, bayan ya ajiye radiyonsa a gafe. Yau dai suka yi alƙawarin za su haɗu da Baby Farha, wacce ta matsa masa kan tana so su haɗu, saboda haka da asuba ya faki idon Maryam ya kai kayan da zai saka shagon waje ya ajiye, sai da ya fita don tafiya aiki ya buɗe shago a hankali ya ɗauka ya tafi, bayan la'asar ya tashi daga aiki, ya je gidansu ya yi wanka ya canza kaya zuwa wanda ya tafi da su ɗin, ya faɗawa Hajiya wurin fatyn abokinsa zai je, ya tafi suna ta waya da Farha tana ba shi kwatancen gidansu. Wani gida babba mai kyau kwatancen ya kai shi, ya same ta tsaye a ƙofar gidan tana murmushi, kallo ɗaya ya gane ta saboda yawan ganin hotunanta, ya sakar mata murmushi yana cewa"Finally yau dai ga ni ga Baby Farha". Tana ƙarewa shigarsa kallo ta ce"Na yi farin cikin ganinka sosai Dear, kallo ɗaya na gane ka duk da kana yi mini rowar hotonka". Ya ce"Ai ga ni, yanzu sai ki yi ta kallona ko?" Ta ce"Ai kuwa dai na ganka". Ta ɗan yi tsaki ta ce"Gidan babu kowa Momy da Daddy sun je unguwa, babu damar mu shiga mu biyu ba sa nan". Ya ce"Babu komai nan ma ya isa, ni dai fatana na ganki dama, tun da na ganki ko yanzu zan iya juyawa". Ta ce"A haba dai". Suna cikin fira sai ga mota ta doso gidan, ta ce"Ga su nan ma sun dawo". Motar tana zuwa dab da su, aka zuge glass, Ali ya duƙa yana gaishe da mutumin dake ciki, ya amsa ya ce"Farha ki shigar da shi ciki mana, bai kamata ki bar baƙo a waje ba". "Ok Daddy" Ta faɗa tana jin mugun daɗi, yayinda matar da suke tare a motar ta haɗe rai ta ce"Wai me yasa kake son biyewa shirmen yarinyar nan ne? Daga ganin yaro ba mu san a inda ta kwaso shi ba sai ka ce ta shigar da shi ciki?" Ya ce"Don Allah Salma ki dinga sassautawa Farha, mene ne idan ta shigo da baƙonta? Tana da inda za ta kai shi da ya wuce nan ne? Ko aurenta ne ya zo ai dai mu za mu aurar da ita ko?" Ba ta sake ce masa komai ba har suka shige gidan, ya bi bayanta da harara yana gyara packing, don ko ma wane mai tsautsayin ne wannan ya zi wurin Farha shi kam yana maraba, don ya zo a gaɓar da yake buƙatar taimakonsa, yanzu zai yi ƙoƙari ya zabewa jakar tsaba, ya gogawa wannan saurin kashin kaji, can su ƙarata, fatansa dai Farha ta ba shi haɗin kai a yi komai cikin ƙanƙanin lokacin ta yadda lissafinsa zai tafi daidai, wayarsa ya ɗakko ya turawa Farha gajeren saƙo ya ce 'Ku gama da wuri kar kishi ya kada ni'. Ya yi murmushi ya shiga falon. Farha ta shiga da Ali ɗakin baƙi, ya zauna, ta je ta kawo masa abinci da lemo, yana ci tana ta yi masa hira, har aka kira magriba ya yi mata sallama ya tafi, bayan ya faɗa mata sai ya dawo za su gaisa da Mom and Dad. Haka ya kwana cike da tunaninta, a firarta ta yau ɗin zancen aure take ta yi masa, wanda shi sam bai shirya ba, ina shi ina auren mace irinta ma? A ina zai ajiye ta? Ya saka a ransa za su taɓa soyayya ne kawai ya ƙara gaba. GIDAN SADIQ Tsawon sati ɗaya ana kallon-kallo tsakanin Sadiq da Kursum, har yanzu bai ce mata komai ba, idan ta kira shi a waya kuma suna gaisawa zai kashe, abun duk ya dame ta, sai a ƙarshen satin ne ya ce mata zai je gidansu, a ranar da fargaba ta wuni, da daddare ya je suka gaisa babu ɓata lokaci ya sanar mata ya yarda da soyayyarta, amma zai duba yiwuwar aurensu, sannan akwai sharuɗan da zai kafa mata idan har ta amince da su, soyayyarsu za ta tafi daidai. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN SADIQ Cikin ƙanƙanin lokaci soyayyarsa da Kursum ta yi ƙarfi na ban mamaki, babu wata magana mai alaƙa da soyayya da take haɗa su idan tana bakin aikinta a gidansa, ko da kuwa aikin kwana Yusra take yi, sai dai idan sun haɗu a yi ta kashewa juna arnen kallo, ga wani sake shiga ran Yusra da ta yi, don kuwa sosai ta tuɓanya kyautatawarta a gareta, yanzu kullum ita ce take yin tuwon dare, Sadiq yana yaba mata sosai a kan daɗin girkinta, kwalliyarta, tsaftarta da kula da yaransa da take yi, ba tare da ya kushe wani hali na Yusra a gabanta ba. A bangaren Yusra kuwa zamansu da Sadiq sabon salo ya ɗauka, ta fita daga harkarsa tsaf, tsakaninta da shi sai magana ta zama ta dole kawai, sam ta daina walwala a gabansa, idan yana falo tana ɗaki, idan ya shiga ɗaki ta koma falo, yana kallo ta koma cikin yaranta take kwana, ita a tunaninta hakan ne zai sa shi shiga taitayinsa ya gane kuskurensa na son kawo wata cikin zuri'arsu, a ganinta matakin da ta ɗauka na fushi zai sanyaya gwiwarsa ya fasa neman auren da yake yi, ya dawo ya rarrashe ta su ci gaba da zaman lafiya, shi kuwa Sadiq ya zuba mata ido nr kawai ya ga gudun ruwanta, so yake sai komai ya daidaita an tsayar da ranar aurensu da Kursum sannan ya sanar mata da wacce zai aura, don ya riga ya sanarwa Hajiya, kuma ta ba shi goyon baya har ma Kursum ta je ta gaisheta, kuma ta yaba da yanayinta. ALI Kai tsaye gida ya wuce, sai da ya yi sallar isha'i sannan ya shiga, ransa fess don ya ji daɗin tarbar da ya samu a wurin Farha. Maryam ta yi masa kallon tsaf ta ce"Ali a ina ka tsaya ka canza kaya, don ba da waɗan nan ka fita ba?" Ya ce"E, na je wurin walimar wani abokina ne, shiyasa na tafi da kayan nan, na canza a gidan Hajiya". Ta ce"Amma ban ga lokacin da ka fita da kayan ba". Yana shiga ɗaki ya ce"Ba ki lura ba ne". Bayan sun ci abinci suka taɓa fira ta ce kanta ciwo yake ta je ta kwanta, ya ji daɗin hakan kuwa, ya janyo wayarsa ya kira Farha tana sauke ajiyar zuciya, suka gaisa ta ce"Da fatan ka ƙarasa gida lafiya". Ya ce"Lafiya ƙalau, my Farha wallahi yau ina cikin shaukin ganinki, komai naki ya yi mini daidai kamar na sace ki na gudu". Ta yi dariya ta ce"Ni ma ka yi mini sosai wallahi komai naka ya burge ni, na san Daddy ma ya yaba da kai, duk da ba mu yi magana ba tukunna". Ali ya yi murmushi ya ce"Na gode sosai Farha, yanzu mene ne mataki na gaba?" Ya ce"Sai na sake zuwa za mu tattauna tukunna". Ta ce"Ya dai kamata a ce ka bar jerin gwauraye don ka fara girma, na san a gida ma an fara gajiya da kai". Ali ya yi dariya ya ce"To kika sani ma ko ina da auren?" Ta ce"Hmm ni ma wataƙil ina da mijin". Ya ce"Habawa kar ki sa jinina ya hau, don kuwa a yau da na ganki ji nake indai ba ke ba sai rijiya". Ta yi dariya, suka ci gaba da waya cike da soyayya, kafin ta yi masa sallama ta ce anjima za su yi chart. Ajiye wayar ta yi, ta sunkuyar da kai, Salma ta ƙaraso a tsanake ta zauna gefen katifar da take, ta ce"Farha wane ne yaron da ya zo wurinki ɗazu?" Tana wasa da yatsunta ta ce"Sunan shi Aliyyu, a whatsApp group muka haɗu, kuma har mun daidaita ma". Salma ta yi mata wani kallo ta ce"A group fa kika ce! Wanda kuka haɗu a group ɗin ne kike zancen kun sasanta? Lallai daƙiƙancin naki ƙara gaba yake". 'Ai ke na gado' Farha ta faɗa a zuciyarta, a fili kuma ta ɓata rai sosai kafin ta ce"To Momy abin da ba kaina farau ba? Nawa ne suka yi aure ta sanadin group?" Salma ta ce"Kuma kin bibiyi auren kin ga yadda zaman ya ƙare?" Farha ta ce"Ni dai ina son shi gaskiya". Salma ta ce"Babu wanda ya ce kar ki so shi, amma haƙƙina ne na kula da rayuwarki, don haka dole na tabbatar da ba shashasha za ki kwaso mana ba, tukunna ma mene ne sana'arsa?" Alhaji Sani da ke laɓe yana sauraron firarsu ya ji an zo gaɓar da kwaɓarsa za ta yi ruwa, don haka ya afko ɗakin yana cewa"To, to, me ake yi babu ni, na ji ana maganar sana'a?" Salma ta kalle shi ta kawar da kai, ba kasafai take son ya dinga zaƙewa a komai da ya shafi Farha ba, ko babu komai ƙanwarta ce, ya kamata ya dinga barinsu suna yin sirrinsu, idan an nemi shi sai ya shiga, ko yanzu rigar bacci ce iya gwiwa a jikin Farha amma ya banko ɗakin babu sallama ba neman izini ballantana ta saka Farha ta suturta jikinta, wannan halin nasa yana ba ta haushi sosai. Ta miƙe tsaye ta ce"Babu komai zancenmu ne kawai". Ya ce"A'a Salma, na sanki sarai, ƙila kin tisa mini ƴa ne kawai da faɗan rashin dalili, me kika yi Farha?" Ya ƙarasa yana kallon fararen cinyoyinta a fakaice. Ta narke fuska ta ce"Daddy a kan baƙona na yau ne fa". Ya ce"Haba Salma, wai ni kam kwaɗa Farha za ki yi ki ci?" Cike da takaici ta ce"Idan kun ga ina jiranka a ɗakinka sai mu yi magana" Ta fice, ta tura yaranta uku da ke falon ɗakin Farha don tare suke kwana, ta kashe kayan kallon da suke yi, ta shiga ɗakinsa ta zauna. Alhaji ya ce"Farhata sana'ar me yaron yake yi ne?" Ta fara sosa kai tana turo masa ƙirjinta da hujja ta ce"Ni ma ban sani ba, amma fa babban ma'aikaci ne Allah". Ya lashi baki daidai sanda yaran suka shigo a hankali ya ce"To anjima za mu yi chart, indai kina son shi magana ta ƙare". "Tanks Daddy!" Ta faɗa tana kwanciya, sannan ya fita. Ta gaji da zaman gidan, tana so ta yi aure ko dan ta daina ƙazamar mu'amalar nan da take yi da mijin yayarta, wacce ta riƙe ta tun tana shekara sha biyu, har zuwa yanzu da take da shekara sha takwas, ta tsaya tsayin daka a kan kula da ita tun bayan rasuwar mahaifiyarsu, duk da mahaifinsu yana raye yana kuma da wata matar amma ta zaɓi ɗauke ƙanwarta ta dawo da ita kusa da ita, saboda ba ta kulawa da farinciki, sai dai shaiɗan ya bugawa mijinta ganga kuma ya taka rawa ta hanyar ƙawata masa Farha da idon sha'a, musamman da ya kasance Salma tana fita aikin koyarwa, ita kuwa Farha ta yi Candy ita kaɗai ake bari a gidan, sai ya yi amfani da wannan damar wurin dawowa daga kasuwarsa ya zo ya dinga ribatarta, tsaf ya siyeta da kuɗi da kuma buɗe mata hanyar barinta ta yi duk abin da take so, tare da gudunmawar shaiɗan ita ma tun tana ganin ba zai yiwu ba har ta yarda, shi ne ya fara saninta a mace, kuma har yanzu da suka ɗauki watanni suna masha'arsu babu wanda ya gane a cikin gidan, to babbar damuwarsa yadda ya lura da sauyin yanayin Farha, kamar mai yaron ciki, don shi kam yana saurin gano mai ciki, idan Salma ta samu ciki shi yake rigata sani, kuma dama ya saba harka da mata kala-kala a waje, wannan wani sirrinsa ne da matar tasa ba ta taɓa sani ba, saboda iya takunsa. A yadda ya lura da rawar kan Farha sosai yake zargin bayan shi ma tana bawa wasu mazan kanta, shi yasa yake son alaƙarsu da Ali ta yi ƙarfi ta yadda ko da cikin ya tabbata sai su ce nashi ne, can su ƙarata, tun da ya san ko giyar wake ta sha ba za ta faɗawa duniya wannan mu'amular ta shiga tsakaninta da mijin yayarta da take taka rawar uwa a gareta ba, shi kuma kowa yake ganinsa kamar ubanta, saboda haka yake son jona ta da Ali ta ƙarfi ko Salma ba ta so. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 HALIMA Satinta ɗaya a gida, kullum sai Haruna ya zo, amma shi yake surutansa ya tafi, hakan ma don kar Umma ta fahimci wani abu ne yasa take zama idan ya zo ɗin, to shi ma ɗin yana zuwa ne kawai don kar ace bai zo ba, amma da za ta yi zamanta har ta haihu sai ya fi son hakan, domin kuwa kwanaki uku da tafiyarta Zainab ta ƙara hillatarsa, ta mantar da shi duk abin da ya faru, suka ci gaba daga inda suka tsaya, ƙiri-ƙiri sun mayar da Baaba ƴar maye, yanzu a cikin fura suke saka mata, kullum da daddare sai ya siyo damammiyar fura, Zainab ta fita ta karɓa, ta cewa Baaba saurayi ta yi mai siyar da fura, shi ne kullum yake aiko mata, dayake Baaba tana son fura duk da ta san ita ce take sakata bacci ba ta fasa sha ba, takan ce ta duwa ta kashe ka gara daɗi ya kashe ka, ta kwankwaɗi furarta ta baje ta yi ta sharar bacci, su kuwa suna can suna baje kolinsu, ƙarshe ma Zainab a can take kwana, don da asuba ma da ƙyar take tashin Baaba ta yi sallah, shi yasa ranta fess take ji, ba ta ma ƙaunar abin da zai sa Halima ta dawo gidan. Baaba ta je ta duba Halima ta kai mata ribar abincinta da Zainab take ta yi, Halima tana ƙirga kuɗin ta ce"Ki cewa Zainab na gode". Baba ta ce"Haba babu komai, to mene ne amfaninta dama idan ba ta yi aikin ba?" Halima ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Baaba har yanzu Zainab tana dama kunun dare? Na yi kewarsa". Baaba ta yi murmushi ta ce"Sai dai na safe, da daddaren dai yanzu wani saurayi ta samo wai yana siyar da fura, to kullum sai ya ƙullo mata ita a dame mai sanyi da zaƙin tsiya". Halima ta ce"Lalllai ashe mun yi suruki, kuma shan furar kuke da daddare? Ai sai ta kashe muku jiki ku yi ta bacci". Baaba ya ce"Sai dai kar a kuma, don wallahi tana kashewa muɗis, Halima idan kika ga baccin da nake kwasa sai ki sha mamaki, wai yanzu sai dai Zainab ta tashe ni sallar asuba". Gaban Halima ya faɗi, dama abin da take son ji kenan, ashe dai Haruna da Zainab ba wuri ta basu don su ji kunya su kaɗai ba, kuma su yi nadama ta har abada, wuri ta ba su saboda su sake samun sakewa da juna, innalillahi wa inna ilaihi raji'un take ta maimaitawa a zuciyarta, kafin ta ce"Baaba don Allah ina roƙonki wata alfarma". Baaba ta tattara nutsuwarta ta ce"To ƴar nan me kike so?" Hawaye ya zubowa Halima ta ce"Yau so nake kar ki sha wannan furar, sannan kar ki bari Zainab ta san ba ki sha ba, ki nuna kamar kin yi bacci da wuri, tsakar dare ki farka ki ga abin da zai faru". Cikin rashin fahimta Baaba ta ce"Mene ne zai faru Halima?" Halima ta ce"Idan kika farka ba lallai ki ga Zainab ba, idan ba ki ganta ba ki duba ta a ɗakina tare da mijina..." Ta ƙarasa da sakin kuka don kar Umma ta jiyo ta. Ƙirjin Baaba ya buga da ƙarfi, tun wancen lokacin da ta kama Haruna da Zainab abun yake damunta, amma ganin Halima ta dawo sai hankalinta ya kwanta, kuma a tunaninta ko kusa Halima ba ta san komai ba a kan wannan badaƙalar. Ta ce"Halima kar dai ki ce mini akwai wani abu da kike zargi tsakanin Zainab da mijinki?" Halima ta share hawaye ta ce"Na san za ki ji abun banbarakwai, kuma bai zama lallai ki yarda da ni ba, amma da za ki yi yadda na ce miki yau ƙila ki yarda". Jikin Baaba ya yi mugun sanyi ta ce"Me yasa kika fara zarginsu?" Halima ta ce"Baaba ya wuce zargi fa, ganinsu na yi ra'ayil aini" Sai ta fara kuka ta ce"Baaba a cikin ɗakina Haruna zai yi mini haka, me na yi masa?" Ta fashe da kuka. Baaba ta ce"Rufa mana asiri ki bar kukan haka, kowane bawa da irin ƙaddararsa, ke kuma taki ƙaddarar kenan Halima, amma na yi miki alƙawarin zan saka ido in sha Allah! Roƙona da ke kawai ki ƙara haƙuri akan wanda kika yi, Halima wannan ba ƙaramin tashin hankali ba ne ka ga mijinka da wata ƙiri-ƙiri, amma ki yi haƙuri duk wanda aka ba shi haƙuri tabbas an cuce shi ne, yanzu yau zan yi yadda kika ce, indai na samu haka ɗin ne yake sake faruwa wallahi na haƙura da zaman gidan nan, zan ƙara gaba saboda ki samu zaman lafiya da mijinki, Zainab tana cutata, ba ta kyauta min ba..." Ta fara kuka. Halima ta share hawaye ta ce"Ki bar kuka Baaba, kuma ba sai kin bar gidan nan ba, domin nima babu tabbacin zan komawa auren Haruna, saboda haka ki yi zamanki, amma ki saka ido kan tarbiyyar ƴarki". Daga haka suka yi sallama Baaba ta tafi jiki a mace. GIDAN SADIQ Sosai Yusra ta azabtu da yanayin zaman nasu, ta gaji, ta ga ya mayar da ita ƴar iska, shi bai yi zancen auren ba, shi bai zo sun sasanta ba, kuma ta kasa gane inda ya dosa, abu ɗaya dai da ta lura shi zaman sam ba ya damunsa, walwalarsa kawai yake yi, ga shi yanzu ya daina ajiye wayarsa ballanta ta gano wani abun, saboda haka yau ta yanke za ta tunkare shi ta ji matsayinta a wurinsa. Da daddare yara sun yi bacci yana ɗaki zaune a gado yana chart ta shigo ta zauna a kujerar mudubi tana yi masa kallon tsaf, tana ƙaunar Sadiq sosai, sam ba ta shirya rabuwa da shi ba ko ba don yara biyu dake tsakaninsu ba, Allah Ya ɗora mata ƙaunarsa. Ta sauke ajiyar zuciya tana harɗe hannunta a ƙirji ta ce"Sadiq!" Ya ɗago daga kallon wayar ya kalle ta ya ce"Na'am Yusra". Ta ce"Ina so ka sanar da ni ma'anar wannan zaman namu, wace ce ni a wurinka? Mene ne matsayina? Sannan ka faɗa min dalilin sauyin halinka". Ya ajiye wayar ya ce"Zamanmu ni da ke zaman aure ne, irin wanda yanayi ya zaɓa nana, ke kuma matata ce, matsayinki yana nan na matata, uwar ƴaƴana, wacce nake so, sannan ni halina bai sauya ba, sauyinki ne ya sa kika ga canzawar nawa". Ta ce"Sadiq ka faɗa mini abin da kake ɓoye mini, wace ce wannan yarinyar da ka fara so? Kuma da gaske za ka iya aurenta? Da gaske ni Yusra za ka iya yi mini kishiya?" Sadiq ya yi murmushi tunowa da badaƙalar da take shirin faruwa gaba kaɗan a gidansa ya ce"Babu wani abu da nake ɓoye miki, yarinyar da nake so kuma idan lokacin da ya kamata ki sani ya yi za ki sani, zancen zan iya aurenta dama ita soyayya ai don aure ake yinta, kishiya kuma ban yi miki alƙawarin dama ba zan yi ba, kin ga kuwa idan kika yi tunanin ba zan iya ba kin yi ragon azanci". Yusra ta girgiza kai ta ce"Sadiq babu wacce za ka aura indai ina raye..." Ba ta ƙarasa ba ya katse ta da faɗin"Ashe kuwa wa'adinki ya zo ƙarshe". Ya tashi ya fice daga ɗakin ya koma falo, ba ya son tattanawar tasu ta yi tsayi har ya faɗa mata maganganun da za su saka ranta ya ɓaci sosai, don ba burinsa ba ne ƙuntata mata. Yusra ta ajiye numfashi, zuciyarta na tafasa, ta bi shi falon, tun kafin ta ƙaraso ya tashi tsam ya koma ɗaki, ta kwanta a kujera tana ayyana abubuwa da dama, a ranar kuwa sun da suna chart da Kursum, wajan sha ɗaya ya gama komai ya saka caji bacci ya ɗauke shi, sha biyu da rabi Yusra ta buɗe ƙofar a hankali, idonta ya sauka a kan wayar tasa da take caji, ta cireta, saɗaf-saɗaf ta fita daga ɗakin ta rufo ƙofar a hankali. Zama ta yi a ƙasan kafet hannunta har rawa yake zuciyarta tana azalzala ta shiga whatsApp chart ɗinsa da Umma ta dubo, ta dinga bi daki-daki, nan ta ci karo da hotunan da ta tura masa, da sauri ta shiga, ƙirjinta ya yi wata irin dokawa bayan ta ga hotunan Kursum tarr, ta shiga kunna voice ta ji muryarta ce fess, zuciyarta ta dinga tafasa, har tana jin kamar numfashinta zai ɗauke, ta fara tunanin da gaske Sadiq Kursum ƴar aikinta yake? Kuma zai iya aurenta? Ta yi ta saƙa da warwara na hukuncin da ya kamata ta yi masa, yanzu yana baccin nan, amma ta taushi zuciyarta daga gurguwar shawarar da take bata, ta dinga screnshote ɗin chart, ta haɗa da hotuna da voice duka ta tura ta whatsApp ɗinta, sannan ta tashi ta shiga ɗakin nasa, ta kunna globe haske ya kawo, tana kallon yadda ya baje yana sharar bacci bayan ya gama zubarwa ƴar aikin gidansa kalaman soyayyar da ya daɗe bai yi wa matarsa ba, ta shiga banɗaki ta ɗebo ruwa ta zo ta sheƙa masa, Sadiya ya tashi a firgice yana innalillahi, ya ce"Yusra ƙalau kike kuwa? Kina cikin hankalinki kika watsa min ruwa?" A fusace ta wurga masa wayarsa, ta ce"Kai ma kana cikin hankalinka ka iya tunanin ka yi soyayya da Kursum? Sadiq ni za ku ci amanata a cikin gidan nan? Me na yi maka?" Sai ta durƙushe a wajen tana kuka sosai. Shi kuwa ya yi tsumu-tsumu na jiƙa shi da ta yi, duk da ya san da zuwan ranar nan amma bai taɓa zaton yau za ta zo ba, ya sakko daga gadon ya zo ya ɗagota, ta fizge tana cewa"Kar ka sake! Kar ka ce za ka sake taɓa ni Sadiq, tabbas yau na yarda namiji ɗan kunama ne, namiji ba shi da kunya sam bai san abun kunya ba, Kursum! Kursum! Da gaske ita ma ta amince tana sonka, kuma za ta aureka?" A sanyaye ya ce"Ki nutsu Yusra, ki fahimce ni soyayyarmu da Kursum ba laifi ba ce, kuma mai tsafta ce wacce muke fatan ta kai mu ga aure, sannan a tunanina za ki fi kowa farinciki, duba da yadda kika santa kika san halinta, kika zaɓota kika ajiye a matsayin wacce za ta kula da gidanki, kin ga ai ta cancanta ne shiyasa kika yi hakan, kuma ni ina ganin idan na aureta ke ma za ki fi sakewa ki yi aikinki, babu tunanin akwai nauyina da na yara ko wani girki da kula da gida, ke kina wajen aiki, ita kuma zan kai yara gidanta, ta kula da mu gabaɗaya, to wannan ba wani abun ɗaga hankali ba ne, to ki nutsu kin ji ko?" Yusra da ta tsaya kamar mutum-mutumi tana kallonsa sai ruwan hawaye da ya ƙi tsayawa, gyaɗa masa kai kawai take yi kamar ƙadangaruwa, sannan ta ce"Na fahimta, kuma na gode, sai dai na san kana sane da ƙudurina a kan kishiya ko? To ina nan akan bakana, muddin za ka ƙara aure sai dai ka rabu da ni". Sadiq ya ce"Da gaske za ki iya rabuwa da ni, ki bar ƴaƴanki?" Ta ce"Ƙwarai kuwa har ma na manta da kai na yi wani auren!". Ya yi ƴar dariya ya ce"Kin ga ni kuwa babu rabuwa da ke a tsarina har abada, kuma jikina yana ba ni ko na Kursum ba zan auri wata, saboda haka ki canza tunaninki". Da ƙarfi ta ce"Ba ka isa ba! Wallahi Sadiq sai ka sake ni, dole ka sake ni! Kuma gobe ko ni ko Kursum wallahi, sai na nuna mata ni ba sa'arta ba ce!". Daga haka ta fice daga ɗakin, ta koma falo ta zauna wasu hawayen suka ɓalle, wani irin raɗaɗi take ji a cikin zuciyarta mara misali, har ta ƙagauta gobe ta yi, Kursum ta zo aiki, wallahi sai dai ƴan gidansu su zo su kwasheta. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: *BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Da asuba Sadiq ya kira Kursum a waya, suka gaisa ya ce"Kursum yau kar ki zo gidanmu aiki". Da mamaki ta ce"Me yasa?" Ya ce"Yusra ta san komai na soyayyar dake tsakaninmu, kuma na faɗa miki yanayin kishinta, to daga yanzu komai zai iya faruwa, saboda haka zancen aiki ya ƙare..." Kamar za ta yi kuka ta ce"Mene ne matakinka a kan hakan? Ina fargabar rabuwarmu". Ya ce"Babu dalilin rabuwa, sai dai ma hakan ya matso da auren kusa, ki kwantar da hankalinki". Kursum ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Allah Ya sa, ka ba wa Anti haƙuri don Allah, ka rarrashe ta" Daga haka suka yi sallama, ta saki murmushi tunowa da yanayin da Yusran take ciki a yanzu, sannan ta kira Sumayya ta larabta mata komai, suka taya juna farinciki. Har gari ya yi haske tana falo a zaune, Sadiq ne ya shirya yaran, ya dafa musu abin da za ci, ko yaran ba su isheta kallo ba ballanta shi, bayan sun tafi makaranta ya haɗa shayi ya kawo mata, ya ajiye a gabanta yana cewa"Yusra ki sha shayi, na kawo miki dankali?" Ta kau da kai gefe ba tare da ta tanka ba. Ya ɗauki kofin ya nufi bakinta da shi, ta tankwaɓe kofin gabaɗaya ya zube a jikinsa, cikin ƙaraji ta ce"Sadiq ka ƙyale ni!" Ya matsa baya yana duba jikinsa da ya ɓaci, ga kuma zafin ruwan shayin. Ya ce"Yusra wannan abin da kike bai dace da ke ba, ni na yi zaton ko a ƙauye an daina irin kishin nan...". A fusace ta katse shi da faɗin"Waye zai yi kishin namiji irinka!? Kar ka sake tunanin kishinka nake yi, dokata ce dai da ka karya nake so na aiwatar da matakin da na daɗe ina faɗa maka, Sadiq ka sake ni tun muna muna biyu, ka sake ni tun guntun mutuncinka da nake gani bai ƙarasa tsiyayewa ba!". Tsayawa kawai ya yi yana kallonta, kafin ya yi murmushi ya ce"Yusra ki nutsu ki yi tunanin da ya dace sai mu yi magana, yanzu ba kya cikin hayyacinki". Ya koma ɗaki, ya yi wanka ya shirya ya fito, har lokacin tana nan inda ya barta ya ce"Mene ne babu a kitchen? Ba za ki fita ba ne, na ga ba ki shirya ba, kar ki yi latti". Ko kallon inda yake ba ta yi ba, ya fice jikinsa a sanyaye ya ƙarasa shago. Yana fita, ta tashi ta ɗakko wayarta lambar Sumayya ta lalubo hannunta har rawa yake ta kirata, Sumayya ta ɗaga tana cewa"Ƙawata ina ta jira ki shigo shiru?" Yusra ta ce"Ok, kin ji labari ne ta wajenta?" Sumayya ta yi murmushi ta ce"Labarin me?" Yusra tana huci ta ce"A ina kika samo wannan tsinanniyar yarinyar Kursum? Ashe matsiyaciya ce zuwa ta yi ta kashe ni da raina, a cikin gidana take soyayya da mijina, wai yau ni Sadiq yake faɗawa zai auri Kursum, wace ce ita!?" Ta ƙasara da daka tsawa har tana buga ƙafa. Sumayya har lumshe ido take saboda farinciki, sai da ta kai aya, sannan ta ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Yusra me kike faɗa haka? Ban fahimta ba ita Kursum ɗin ce take son Sadiq?" Yusra ta ce"Suke son juna dai, yanzu haka zancen aure suke yi, aure fa da ƴar aikina..." Ta fashe da kuka. Sumayya ta ce"Ki yi haƙuri, idan kin shigo asibiti za mu yi magana". Yusra ta ce"Ba zan iya fitowa ba yau, kin san halin da nake ciki kuwa?" Sumayya ta ce"Ok, idan na tashi zan shigo, ki kwantar da hankalinki pls, wannan ƙaramar matsala ce". Wani baƙinciki ya rufe Yusra, yanzu wannan ce ƙaramar matsala? Matsalar da za ta yi sanadin rabuwa da mijinta da ƴaƴanta? Ta share hawaye tana jiran zuwan Kursum ɗin. Har sha biyu ta yi, tana nan zaune a wurin, zuwa yanzu ta san Kursum ba za ta zo ba, don haka ta sake cika ta yi fam! Yaran suna dawowa daga makaranta suka fara buga gidan cike da zumuɗin ganin Anti Kursum domin su nuna mata yadda suka cinye home work ɗin da ta taya su, Yusra tana buɗe musu suka faɗa, har suna rige-rigen shigewa ciki, Fanan ce ma ta tsaya a tana cewa"Momy ba ki je aiki ba?" Ita kuwa Afna ba ta bi ta kanta ba, Yusra ta bi su da kallo ganin sun shige da gudu suna kiran Anti Kursum, ta girgiza kai ta bi bayansu, hannu ta harɗe a ƙirji tana kallonsu ganin jikinsu duk ya yi sanyi suna raba ido, Fanan ta ce"Momy yau Anti Kursum ba za ta zo ba?" Afna ta ajiye jakarta tana ɓata rai ta ce"Kuma shi ne ba ta faɗa mana yau ba za ta zo ba, kin ga Momy ita ta ce idan muka cinye home work za ta ba mu chocolate as gift, ki kira ta a waya pls!". Yusra ta zauna tana sauke ajiyar zuciya, duk suka zauna rakuɓe cike da damuwa. Ƙarfe ɗaya Sadiq ya kira ta a waya, sai da ya yi mata kira uku sannan ta ɗauka, kai tsaye ya ce"Kina gida ko kin fita? Idan zan samu abinci a kawo min pls". A fusace ta ce"Ina gida kuma ba zan dafa ba! Ka kira wacce ta fi ni komai ta dafa maka". Ta katse wayar tana cewa"Aikin banza kawai, ni za a yi wa bariki a cikin gidan nan?" Tana rufe baki Fanan ta ce"Momy yunwa" Afna ta ce"Ni ma Momy pls". Ta daka musu kafirar harara ta yi ƙwafa, tana jinjina kai. Babu jimawa Sadiq ya shigo gidan, ya san tun da ta ce ba za ta yi girki ba, da gaske ba za ta yin ba, shi yasa ya dawo saboda ya ga yadda yaran suke, yadda ya bar komai a haka ya same shi, kayan miyan da ya kawo mata suna inda ya ajiye, ɗakin kaca-kaca sai yaran da suke zaune da unifom a jikinsu, ya ƙarasa ya zauna a kusa da su da murmushi ya ce"Kun dawo? Me yasa ba ku cire unifom ba?" Duk suka yi shiru, ya ce"Kun ci abinci?" Suka girgiza masa kai. Ya tashi ya ɗauki kayan miyan ya shiga kitchen, sai ya ga akwai sauran miyar jiya, ya ɗora farar taliya, ya dawo ya canza musu kaya, tana dahuwa ya zubo musu, shi ma ya zuba suna gama ci ya yi musu wanka da shirin islamiyya, suna shirin ficewa daga gidan sai ga Sumayya ta shigo, kallo ɗaya ya yi mata ya kauda kai, ta buɗewa yaran hannu tana yi musu oyoyo, suka ƙarasa wurinta don sun santa, ta rungume su tana cewa Sadiq"Oga ina wuni? Makaranta za a miƙa su?" "E" Kawai ya ce ya fice daga gidan, ta ɗakko kuɗi a jakarta ta ba su ta ce su ta ce"Ga shi ku sayi alawa ko". Suka yi mata godiya suka fice. Da sallama ta ƙarasa falon, Yusra ta amsa ba tare da ta juyo ba ƙwalla tana cika idonta, Sumayya ta ƙaraso ta kwashe kwanukan dake zube a falon ta kai kitchen, sannan ta dawo ta share tass, ta kalli Yusra da alamun tausayawa ta ce"Kin ci abinci ko?" Yusra ta girgiza mata kai, wanda ya yi sanadin zubowar hawayen, tsam Sumayya ta shiga kitchen ta haɗo shayi, ta zubo taliyar ta kawo mata, babu musu ta ɗauke kofin shayin tana sha a hankali har ta shanye, ta ce"Sumayya haka Sadiq zai yi mini?" Sumayya ta ce"Ki ci abinci tukunna". Yusra ta ce"Na ƙoshi!". Sumayya ta ajiye numfashi mai nauyi ta ce"Wai ƙawata me kike yi har haka ta faru? Amma lallai Sadiq ya yi mana bazata, idan ban da namiji a ce mutum yana da mace kamar ki har ya iya kallon wata, watan ma ƴar aiki? Yanzu kina ga wannan ba janyo mana raini ba ne idan duniya ta ji mijinki zai auri ƴar aikinki? A wace irin mace za a kalle ki? Kai mata suna ganin takaicin ɗa namiji!" Ta ƙasara kamar za ta yi kuka. Sannan ta ce"To wai ma ta ina za ki fara kishi da ƙasƙantacciya irin Kursum?" Yusra ta haɗiyi yawu mai ɗaci ta ce"Sumayya maganganunki suna ƙara ƙona zuciyata ne kawai, kina fusata ni, kar ki sa na je har gida na shaƙeta, ki ba ni shawara kawai!". Sumayya ta ce"Shawara ɗaya ce, kuma duk mai sonki ita zai ba ki, babu ta yadda za a yi fa ki zubar da ajinki wurin kishi da mara class irin Kursum, za ki ja mana abub faɗa har a wurin aikinmu, kowa zai raina ajinki a ce kin kasa riƙe mijinki har ƴar aiki ta ƙwace shi, sannan irin yaran da za su yi haka ina tabbatar miki shaiɗanu ne a cikin mata, ƙarshe indai kika zauna da ita baƙinciki ne zai yi ahalinki, don kina kallo za ta ƙwace gidan". Yusra tana hawaye tana jinjina kai, alamar duka ta gamsu da maganganunta, Sumayya ta ɗora da faɗin"Kina da mafita guda biyu don kare mutuncinki! Na ɗaya ko dai ki bar aikinki bari na har abada, ki duƙa ki nemi sasanci da Sadiq ki shawo kansa ya fasa auren, ki zauna a gida ki dinga kula da shi da yara, ko kuma ki haƙura da aurenki ki sa ya sake ki, tun kafin ya yi auren tonon asirin nan da yake shiri, kin ga idan aka yi haka babu me cewa ƴar aiki ta ƙwace shi, don dama kun riga kun rabu ya sake ki, kin ga kenan shi duniya za ta zaga a ce ta ƙare masa ya auri ƴar aiki, ke kuwa ajinki ya kai ki yi wani auren na kerewa sa'a ki auri wanda zai ba ki farinciki, ki tattarawa Sadiq ƴaƴansa ki ba shi shegiyar Kursum ɗin da ya zaɓa ta riƙe, ke kuwa kina can kina amarcinki hankali kwance, ki fita aiki babu wata hidima mai yawa a gabanki, tun da daga ke sai shi". Yusra ta yi shiru tana nazari, Sumayya ta ce"Wanne kika zaɓa?" Ta sauke numfashi ta ce"Kin fi kowa sanin ba zan bar aikina ba, haka kuma ba zan zauna da kishiya ba har abada!". Sumayya ta ce"Kina da gaskiya Yusra, Sadiq ya ci amanarki, ya nuna miki butulci tsantsa, ya kamata ki nuna masa za ki rayu ko da babu shi, kuma rayuwa mai inganci, amma tsakanin mata da miji sai Allah, kar na zaƙe da yawa ban san zuciyarki ba". Yusra ta ce"Kina ganin haka zan bar Kursum ta shayar da ni wannan maɗacin ta ci bulus?" Sumayya ta ce"Sadiq ne ya shayar da ke maɗaci fa ba ita ba, don duk wata ɓaraka daga wurinsa take, to ni ban ga laifinta a nan ba, ba ki san mazan zamanin nan! Ki godewa Allah ma da aurenta zai yi ba lalata suke yi miki a cikin gida ba, kin manta sister Hafsa da mijinta ya yiwa ƴar aikinta ciki, har ta kawo ta asibiti muka zubar? Ko kin manta sister Asiya da mijinta ya dinga lalata da ƴar'uwarta ta jini, sai da aka kai matakin da ta kama su ido da ido? Idan kika kalli wannan ke naki ai mai sauƙi ne, ki rabu da ita, don kula ta ma zubarwa da kanki aji ne kawai, ni yanzu daga nan gidansu zan wuce, uwarta ma yau sai na yi mata tass, sai sun yi nadamar sanina a rayuwarsu". Yusra ta jinjina kai, Sumayya ta tashi ta ce"Bari na tafi, yanzu abin da nake so da ke, ki bi komai a hankali, ba sai da tashin hankali zai sake ki ba, ko kutu za ki iya kai shi, ki saki ranki ki dinga komai yadda kika saba, har sai kin ga batun auren ya zo sai ki tada ɓalli ko kuma ki tafi gidanku". Yusra ta tashi ta ce"Na gode sosai Sumayya, zan yi yadda kika ce in sha Allah!". Ta ce"Yawwa, ki daure zuciyarki, yanzu ki gyara gidan ki yi girki, sannan gobe ki shigo aiki, kuma a nutse pls kar hankalin munafukai ya fara kai wa kanki". Yusra ta gyaɗa mata kai, tana gamsuwa da shawararta. Bayan ta tafi, ta ci taliyar, ta shiga gyaran gidan, ta ɗora girki sannan ta yi wanka ta yi sallah ta kwanta, tana gama girkin ta yi guntun bacci, bayan la'asar ta tashi ta ci abinci ta zauna tana ta bitar kalaman Sumayya zuciyarta na ƙara zafi. Har yara suka dawo daga makaranta, yanzu ma babu walwala a fuskarta ta canza musu kaya, ta zuba musu abinci suka ci, tana kallo suka ɗakko jaka suka yi home work ɗinsu suka gama, tun kafin isha'i suka je suka kwanta ko shimfiɗa ba ta gyara musu ba. Ana idar da sallar isha'i Sadiq ya dawo, lokacin har ta yi shimfiɗa ta kwanta a falo, ya shiga ɗakin yara ya ga sun fara bacci, ya duba kitchen ya ga ta yi girki, sai hankalinsa ya kwanta, don dama tunanin abin da yaran za su ci ne ya dawo da shi, abincin ya zuba ya zauna ya ci a kitchen ɗin, yana gamawa ya yi wanka a gaggauce ya shirya ya tafi gidansu Kursum. GIDAN HARUNA Jiki a sanyaye Baaba ta koma gida, ji ta yi kamar ta rufe Zainab da duka sanda take tambayarta ya jikin Halima, ta daure tana biye da take-takenta, tana kallon lokacin da aka kira ta a waya, ta tashi za ta fita Baaba ta ce"Ina zuwa?" Zainab ta ce"Ɗan albarkanki ne ya yo aiken fura". Baaba ta gyaɗa kai, Zainab tana shigowa ta ji Haruna ma ya shigo ya yi ɗakinsa, Baaba ta ce"Ɗaya kenan!" Zainab cikin rashin fahimta ta ce "Baaba mene ɗaya?" Baaba ta ce"O'o! Babu komai, zancen zuci ne". Zainab ta ɗauki kofina biyu ta fita da fura, don dama kullum a waje take juyewa ta saka mata maganin wanda hakan bai taɓa sa Baaba ta yi wani tunani ba, a hankali ta leƙa ta gefen labulen ta kuwa ga sanda Zainab ta haɗa komai na maganin da suke banka mata, ta koma ta zauna tana goge ƙwallar mamakin wannan zamanin da suke ciki, ace jikarta ce za ta mayar da ita ƴar maye? Zainab ta shigo ta ajiyewa Baaba tata a gabanta tana cewa "Ga ta nan Baaba kar ta huce". Baaba ta ce"Ke don ubanki ɗakko min muhucina a gindin murhu, kullum a can kike baro shi ki bar ni da lalube cikin dare". Tana fita Baaba ta ɗauke furar ta Zainab ta mayar mata da tata inda ta Zainab ɗin take, don kofunan kala ɗaya ne, tana ajiye mata maficin ta ɗauki fura ta kwankwaɗe, yayinda Baaba ta sha mara magani a zuciyarta tana cewa 'yau na ga tsiya'. Babu jimawa Zainab ta fara jin bacci mai nauyi, tun tana kokowa da shi har ya rafketa, ta kwanta tuni ta yi wata duniyar, Baaba tana zaune tana kallonta lokaci-lokaci tana share ƙwallar tausayin rayuwar Zainab ɗin, har aka ɗauki lokaci, sannan ta tashi ta ɗauki mayafin Zainab ta lulluɓa ta fito ta fara ƙwanƙwasa ɗakin Haruna, yana falo a kwance, cikin ƙaguwa ya ce"Zee shigo mana!". Baaba ta tura ƙofa ta shiga, Haruna ya taso ya rungume ta yana cewa "Yau kin latti, i miss you". Baaba ta ce"La ai yau ita ce ta sha furar shi ne na ga da a barka haka a gantale gara ni na zo". Da wani mugun firgici Haruna ya sake ta, yana faɗin"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!". LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 ALI Ya daɗe a zaune kafin ya tashi ya yi wanka, ya shirya cikin manyan kaya don ganawa da surukinsa ya fice, gidan su Maryam ya nufa, yana tafe yana tunanin abin da zai ce idan ya je, gefe guda kuma yana ayyana Maryam ba za ta iya tona masa asiri ba, musamman da ba ta da tabbas a kan shi, sai zargi mai ƙarfi, a shago ya tsaya ya sayi kayan shayi da biredi sannan ya ƙarasa gidan, yanzu ma da ya kira ta ba ta ɗauka, layin nasu shiru babu gilmawar yara, da alama duk sun tafi makaranta, hakan ya sa shi kutsa kai ciki ya tsaya a zaure yana rafka sallama, daga cikin gidan maman Maryam ta amsa, ya shiga da wata sallamar, ta saki fuska ta ce"Ashe Ali ne, sannu da zuwa, ƙaraso". Ya bi bayanta zuwa falon gidan, suka zauna suka gaisa, kafin Maman ta ce"Ka biyo ta kenan, ɗazu sai ga ta da duku-duku, ana fitowa daga masallaci, gabana ya faɗi sosai, nake tambayarta mene ne ya kawo ta, ta ce tana zuwa, ta yi alwala ta yi sallama ta kwanta to ga dai ta can har yanzu ba ta tashi ba". Ali gabansa sai faɗuwa yake yi, duk da dai ya ji dama-dama da ba ta faɗa ba tukunna, ya ce"E...Ai Mama ba wata matsala ba ce, kawai ɗan saɓani ne muka samu a daren jiya, to ban san ma ta fusata har haka ba, da na ga na yi ta ba ta haƙuri, sannan ta nuna kamar ta haƙura, to na dawo daga masallaci kawai na tarar ba ta nan, tun da nan ta zo ai babu wata damuwa Mama, a rabu da ita ta huce". Mama ta ce"Oh! Maryam an yi shashasha wallahi, ka yi haƙuri bari ta tashi na ji ta bakinta, ai babu zancen a rabu da ita, dole ta koma, dama shi zama kowane iri ne ai ya gaji haka, za a ɓata maka, kai ma za ka ɓatawa mutum, ku dinga haƙuri da juna duk wanɗanda kuka ga sun zauna lafiya to a haka suke, sai haƙuri". Ali ya ce"Babu komai Mama, ya wuce in sha Allah! Ga wannan" Ya ƙarasa maganar yana miƙa mata ledar hannunsa, sannan ya tashi ya fice tana yi masa godiya. A gidansu ya karya yana faɗawa Hajiyarsa yau ba zai je aiki ba, akwai inda zai raka abokinsa, bayan ya gama ya yi zamansa a nan, ya sake kira Maryam ba ta ɗaga ba, sai ya tuna an ce tana bacci, ya tura mata gajeren saƙo mai ɗauke da ban-haƙuri da kuma roƙonta kar ta faɗawa kowa matsalarsu, za su zauna su sasanta. Tana tashi kuwa ta ga kiransa da saƙon, ita ma ba ta da niyyar tona masa asiri, ta tauna tsakuwa ne kawai don aya ta ji tsoro, sannan tana ganin idan ta yi nesa da shi zai nutsu ya san muhimmancinta. Ta fito ta yi brush suka gaisa da Mama, ta miƙa mata leda ta ce"Mijinki ya zo kina bacci". Maryam ta kalle ta da mamaki ta ce"Mama me ya ce?" Mama ta galla mata harara ta ce"Ban sani ba!" Daga haka ba ta sake cewa komai ba, ta tashi ta zubo ruwan shayi ta karya, tana gamawa ta koma gefe ta raɓe saboda ta ga Mama ta ƙi sakar mata fuska, wayarta ta ɗakko don ta duba saƙon jiya ta sake bibiya ko za ta sake ganin wani abu da ba ta fahimta ba, amma sai ta ga wayam babu saƙon kwata-kwata, ta san shi ya goge, sai kawai ta girgiza kai, wajan sha ɗaya ta ga Mama ta fara hada-hadar ɗora girki, don haka ta fita tana taya ta aikin, a bazata ta ji maganar Maman ta ce"Maryam rayuwar aure fa haƙuri ce, duk wanda ya ce zo mu zauna to fa kamar ya ce zo mu saɓa ne, saboda dole za a saɓa ɗin, to haƙuri da fahimtar juna ne zai taƙaita saɓawar, wannan akwatin da kika ɗakko babu muhallinsa a gidan nan, domin kin san idan babanki ya ji kin zo dole ki koma a yau, shi yasa ban ma faɗa masa ba, don haka ba na so ya dawo ya same ki, da la'asar za ki shirya ki koma ɗakinki, ba na son sakarci". Lokaci ɗaya idonta ya kawo ruwa, ta fara hawaye kafin ta ce"Mama ba ku san me ya yi min ba fa". Mama ta ce"Me ya yi miki? Ko me ya yi miki ai yaji ba mafita ba ne, zama za ku yi ku fahimci juna, kuma ya ce ya ba ki haƙuri, har kika damu mijin da zai yarda ya yi miki kuskure ya ba ki haƙuri Maryam amma kike son ɓata rawarki da tsalle? Na san fa halinki sarai, Ali yana sonki sosai zai yi wuya ya dinga yin abin da zai ɓata ranki haka siddan, ƙila ma ke ce mai laifin". Zuciyarta ta dinga ƙuna, ta ƙi cewa komai, har Mama ta yi faɗanta ta gama. Ƙarfe goma sha biyu Ali ya tashi ya tafi gidansu Farha, zuciyarsa tana bugawa, duk da dai Farha ta faɗa masa Daddy ya ce ya yaba da hankalinsa, kuma shi ba mutum ba ne mai tsauri, kawai ya tabbatar duk abin da zai faɗa masa gaskiya ne, da wannan ya ɗan samu sassauci, har ya samu ƙwarin gwiwar zuwa, duk da yana ayyanawa a ransa wannan ne ma zai zama zuwansa na ƙarshe, don idan suka ji cewa shi kafinta ne bai zama lallai su ba shi ƴarsu ba. A ɗakin baƙi aka sauke shi, Farha ta cika shi da kayan ciye-ciye tana ta farinciki, ƙarfe ɗaya saura kwata Daddy ya shigo suka gaisa a mutunce, sannan ya ce su je masallaci su dawo. Bayan sun dawo, suka ƙara gaisawa sosai, kafin Ali ya sad da kansa ƙasa yana jiran ta inda Daddy zai fara, gyaran murya ya yi ya ce"To ni dai sunana Alhaji Sani, kuma ni ɗan kasuwa mai had-hadar kaya kala-kala, ko'ina za ka iya samun mu, ban sani ba ko Farha ta faɗa maka alaƙarmu? Ba ni ne mahaifinta ba, ni mijin yayarta ne kawai, amma a yanzu ni ne mai taka rawar mahaifin nata cikin rayuwarta, muna saka ido akan shige da ficenta sosai ni da yayarta, duk da yarinya ce mai nutsuwa". Ya tsagaita, sannan ya ci gaba,"Ranar da na fara ganinku a ƙofar gida na tambaye ta waye kai, ta ce kana sonta da aure ne, to na lura da nutsuwarka, shiyasa har na kira ka don mu tattauna, ina so ka faɗa mini wane ne kai a taƙaice". Ali ya sauke ɓoyayyiyar ajiyar zuciya ya ce"Sunana Aliyyu Ibrahim, mahaifina ya rasu watannin baya, sannan idana aure, amma babu yara, kasancewar ma ba a daɗe da yin auren ba, kuma sana'ata shi ne kafinta, da ita nake gurgura rayuwar gidan nawa". Daddy ya yi shiru na sakanni kafin ya jinjina kai ya ce"Madallah! Amma Aliyyu yanzu ka shirya ƙara wani auren kuma kana ganin za ka iya riƙe mata biyu da wannan sana'ar?" Ali ya ce"E to, gaskiya ni ma ina ta tunanin hakan, amma indai ba gaggawa ake wurin auren Farha ba, babu matsala zan iya neman wata sana'ar na dinga yi mu ga abin da Allah zai yi nan da shekara ɗaya". Daddy ya yi masa wani shashashan kallo, ba tare da Alin ya lura ba, saboda kansa a ƙasa yake, ka sauke ajiyar zuciya ya ce"Aliyyu ba zai yiwu Farha ta ƙara shekara ɗaya babu aure ba, idan har kana sonta to ya zama wajibi da auren da komai ya wakana nan da watanni biyu kaca!". 'An zo daidai wajen' Cewar Ali a zuciyarsa. A fili kuwa gyara zama ya yi ya ce"Daddy ka ga a yanayin ƙarfina ba abu ba ne mai sauƙi na tara kuɗin aure nan da wata biyu, yanzu haka ma fa a gidan haya nake da matata, kuma a yanayin Farha kamar ba ta taso a rayuwar matsi ba, bai dace na kai ta gidan haya mara yalwa ba, to a son samuna ko da ban gina mata gida ba, na samar mata gidan haya wanda zai yi daidai da rayuwarta, saboda haka wata biyu ya yi mini kaɗan, mu dai bar shi a shekarar". Daddy ya ce"Aliyyu kana son Farha?" Ali ya gyaɗa kai alamar yana sonta. Ya ce"Naira nawa zan ara maka ka yi komai na auren cikin wata biyu a ɗaura?" Ali ya ji ƙirjinsa ya buga, ya ce"Daddy ka manta yanayin sana'ata, da kuma nauyin iyali da yake kaina? Aron kuɗi bai dace da ni ba, don bai zama lallai na samu hanyar biyansu a sanda ake buƙata ba". Daddy ya ce"Ai ni ne na ce zan baka, kuma kuɗin nan za ka biya ne a hankali ko nan da shekara uku ne, sannan zan samar maka gurbi a wani shagona a kasuwa". Ali ya yi shiru yana nazari, sannan ya ce"Daddy a ba ni lokaci zan yi shawara da mahaifiyata, duk yadda muka yanke zan zo na sanar maka, na gode sosai". Ba don ya so hakan ba ya ce"To babu damuwa, ina saurarenka". Daddy yana fita Farha ta shigo, Ali ya bi ta da kallon burgewa, a zuciyarsa yana ayyana dole ya bar ta nan ba da jimawa ba, cike da nishaɗi take jansa da fira, yana amsa mata sama-sama, har ta gane akwai matsala a yanayinsa, ta tattara hankalinta gare shi ta ce"Aliyyu, ya kuka yi da Daddy?" Ali ya ce"Za ki ji komai daga bakinsa ai, ni bari na wuce wurin sana'ata". Suka yi sallama jiki a sanyaye ya tafi, a ɗakin ta ɗauki waya ta kira Daddy, bai ɗauka ba ya tura mata saƙo ya ce ta shigo ciki za su yi magana duka har yayarta, don haka ta tashi ta tafi ɗakin. A firgice Farha ta miƙe sanda Daddy ya zo gaɓar ƙarshe a bayanin da yake musu na wane ne Ali, ta ce"Allah Ya kiyaye! Wallahi tallahi ba zan auri kafinta ba, har ma yana da mata, kuma a gidan haya, amma Daddy kake iya kallona kana faɗa mini za ka ara masa kuɗi ya aure ni? Tsakaninka da Allah idan ƴarka ce za ka iya yi mata haka!? Sai ni da ka raina?" A tsawace take maganar riƙe sa ƙugu kai kace ɗanta ta saka a gaba take yi masa faɗa. A fusace Salma ta tashi ta ce"Farha ba ki da hankali ne!? Mene ne ya hau kanki da kike faɗawa Alhaji haka? Akwai abin da ba ya yi miki wanda yake yi wa ƴaƴansa da har za ki yi zaton ba zai so ci gabanki ba? Lallai kin cika butulu!" Farha ta ce"Idan na butulcewa wannan mutumin har meye? Ke ma ƙaddara ce ta sa kika aure shi, amma sam ba mijin zama ba ne...". Kafin ta rufe baki Salma ta ɗaga hannu za ta mareta, ta cafe hannun tana cewa"A'a fa Momy, gaskiya na wuce duka a gidan nan" Ta yarfar da hannun nata. Ta ce"Daddy ka kira shi salun-alun ka faɗa masa ba zai samu aurena ba, don wallahi ko sama da ƙasa za ta haɗe ba zan auri matsiyaci ba!" Daga haka ta shige ɗakinta ta bar su daskare da mamaki musamman Salma. Shi kuwa Ali kai tsaye gidansu ya wuce, ya kwashe komai ya labartawa mahaifiyarsa, nan take ta rufe shi da faɗa kamar za ta dake shi ta ce"Kuma yanzu saboda kai shashasha ne har kake neman shawara!? Wane aure za ka yi bayan aurenka ko shekara bai yi ba? Kuma Maryam uwar me ta yi maka da har za ka fara hangen wata a waje? To wallahi ko za ka yi aure ba dai yanzu ba, kuma ba dai wannan yarinyar ba, ka ɗakko mana kara da kiyashi haka kawai ta dinga kallonmu kamar kashi? Har a ara maka kuɗi ka aureta, sai ka ce ana neman kai da ita? To wallahi kar ka sake na ji ka sake zuwa gidan ma, kuma kar ka sake ka karɓi aiki ko ya baka, ka faɗa masa aure babu shi!". Daga haka ta fice ta bar shi a ɗaki ta hau harkokinta. Ya daɗe a zaune kafin ya tashi ya fice, a ƙofar gida ya zauna ya kira lambar Maryam, ba ta ɗauka ba, ta yi masa tex ta ce muddin ya zo gidansu yau sai ta tona masa asiri, yana karantawa ya tura mata amsar ta yi haƙuri. Dab da magriba yana zaune a ƙofar gidan Hamza ya zo wucewa, ya zauna suka gaisa, kafin tsaki ya kufcewa Ali, Hamza ya ce"Mutumina ya dai?" Ali ya ce"Babu komai yanayin rayuwar ne kawai". Hamza ya ce"A don Allah ka faɗa min, na lura kana cikin damuwa". Ali ya ce"Wallahi matsala muka samu da Maryam tana gidansu, ban san ranar dawowarta ba". Ga mamakinsa sai ji ya yi Hamza ya ce"Alhamdulillah!" Ali ya yi masa wani mugun kallo kafin ya ce"Me kake nufi?" Hamza ya ce"A babu komai, gani na yi mene ne naka na damuwa? Yanzu ai kai sai dai a taya ka murnar samun ƴancin kanka, ka rabu da takunkumi". Ali ya ce"Ni na ce maka matata takunkumi ce a gare ni?" Hamza ya ce"Har sai ka faɗa? Ni taimako ɗaya za ka yi min don Allah ka ba ni aron gidan naka ko falo ne". Ali ya ce"Ka yi uwar me a gidana?" Hamza ya ce"Wallahi wata yarinya ce muka yi da ita za mu haɗu anjima kaɗan, to kuma ga shi dama kuɗin hannuna babu auki, kama hotel wahala ce, ka san gidana yanzu ƴan haya ne a ciki, tun da aka kai wa Baba tsegumin ina kawo mata, ya ce idan ba zan dawo da matata ba na tattara na koma gida da kwana, a dole na koma aka saka ƴan haya a gidan, ka gan ni yanzu ba ni da madafa". Ali ya ce"Haba Hamza, yanzu gidan nawa na auren sunna kake so na bari ka kai wata ƙazama har cikin ɗakin matata?" Hamza ya ce"A'a ni fa ban ce zan hau maka gado ba, ni ko zaure ka ba ni ma na gode wallahi". Ali ya ce"Ba zai yiwu ba". Hamza ya tisa shi a gaba da magiya, kamar wanda ya asirce Ali sai ya amince, tun da yana ganin ai Maryam ba za ta dawo yau ba. Bayan sallar isha'i Hamza da buduruwarsa suna cikin gidan Ali, a falo shi kuma yana ƙofar gida a zaune yana jiransu, tunani ya cushe masa kai, yanzu suka gama waya da Farha ta faɗa masa ba za ta aure shi ba, ta kuma ci masa mutunci kamar ba ita ba, sai dai shi har zuciyarsa ya kwalaitu da aikin da Daddy ya ce zai ba shi, kuma yana tunanin indai aure ya fasu babu zancen aiki, ga zaman Maryam a gida sam ba ya so, kar a ja ra da zance ra fasa ƙwai kowa ya san halinsa. Bai ankara ba ya hango Maryam tafe da akwatinta tana tunkaro shi, gabasa ya bada rass! Ya miƙe tsaye yana cewa"Maryam ya aka yi kuma kika dawo yau?" Maryam da take cike da baƙinciki na koro ta da Baba ya yi, ko kallonsa ba ta yi ba ta sa kai za ta tura ƙofar gidan, Ali ya tare da sauri yana cewa "Ɗan tsaya tukunna, mu je na siyo miki tsire ko balangu, amarya ai sai da mai yaji ko" Ya ƙarasa da dariyar yaƙe. Maryam ta yi tsaki cike da takaici ta tura ƙofa ta shige gidan tana jan akwatinta, Ali ya ɗora hannu a ka, yana jin kamar ya fasa ihu. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Haruna ya ja baya zuciyarsa na ta bugawa, Baaba ta fashe da kuka ta ce"Yanzu kai tsakaninka da Allah ka kyautawa kanka, ka kyautawa Halima?" A raunane ya ce"Ki yi haƙuri Baaba, an yi na ƙarshe in sha Allah!". Baaba ta ce"To dama na ƙarshe mana, ba sai ka sake ganinmu ba ma, ballantana ka lalata ƴata? Ka je ka yi, duniya ce ta ishi kowa riga da wando". Daga haka ta fice, tana shiga ɗaki ta ɗauki mafici ta dinga rafkawa Zainab, Zainab da bacci mai nauyi yake kanta, ta tashi a firgice tana kare kanta da hannu, "Wayyo Baaba me na yi miki!?" Ta tambayeta tana shigewa kusurwar ɗakin. Baaba ta ci gaba da dukanta tana cewa"Ubanki kika yi mini, Zainab ashe da na kama ku da wancen ɗan busurun Haruna, bai sa kin ji kunya kin fita hanyarsa ba? Ke wace irin mahaukaciya ce Zainab?" Sai ta yi jifa da maficin ta zauna ta fashe da kuka tana cewa"Ke dai kin zama zakka a cikin ahalinmu, wallahi ba zan iya ba gara na mayar da ke yadda na ɗakko ki, ruƙonki sai Audu, ki koma ya ci gaba da dukanki kamar jaka!" Daga haka ta tashi ta fara birkito kayan sakawar Zainab ɗin tana watsa su a tsakar ɗakin. Hankalin Zainab ya yi bala'in tashi, don ba ƙaramin jin daɗin zaman wurin Baaba take ba, ta fashe da kuka ta je ta riƙe hannunta ta ce"Don Allah Baaba ki yi haƙuri, wallah na daina ba zan sake kula shi ba". Baaba ta fizge ta ce"Sake ni ja'irar banza da wofi, gobe tun farar safiya zan kai ki gidan Audu haka kawai kin hana ni na zauna mutu a ɗakin mijina, na barwa kishiyoyina gida, alhalin ni ce uwar gida, kin sa ina yawon haya, to wallahi ba zai yiwu ba!". Ita dai Zainab hawaye take ta yi, sai da Baaba ta gama mita ta gama ta kwanta ta fara bacci, sannan ita ma Zainab ta kwanta, sai kuma ta tashi ta fara tattara kayanta da suke ƙasa, firgigit Baaba ta miƙe tsaye tana cewa"Munafuka ina za ki je" Zainab ta ce"Kayana nake gyarawa fa". "Kwanta!" Cewar Baaba cikin daka tsawa, Zainab tana kwanciya Baaba ta ɗakko ɗan kwali biyu ta haɗe su ta ƙulle ƙafarta da ta Zainab, sannan ta kwanta tuni bacci mai nauyi ya suri Zainab". ALI Sati ya yi cif bai koma gidan Hajiya ba, duk yadda take ta yi masa naci, sai dai su yi waya kawai idan yana wajen aiki, lallaɓa Maryam yake yi a yanzu, yana so ta sakankance da shi ta cire zargin komai a ranta, kuma Alhamdulillah sun samu daidato a kwanakin, ana magriba yake dawowa gida su yi ta firarsu, idan ka ga ɓacin ranta to dare ya yi ya buƙaceta ne, yanzu ransa zai ɓaci wataran ma sai ya yi nadamar kulata, shi yasa kullum cikin azabtuwa da kewar Hajiya yake, abun har mamaki yake ba shi wai ya fi shaukin kasancewa da babbar mace fiye da yarinya shakaf irin Maryam kuma masoyiyarsa. A rana ta takwas ne suka yi da Hajiya zai kawo mata ziyara, ai kuwa tun a waya kalamanta suka saka shi farinciki da zumuɗi, ana idar da sallar la'asar ya tashi daga aiki ya tafi cike da ɗoki, Hajiya ta tare shi da murna tana nuna masa yadda ta yi kewarsa a bayyane, bayan magriba ya ci abinci ya yi wanka ya yi ɗaiɗai a falo tamkar mai gida, Hajiya ta kalle shi cike da ƙauna ta ce"Aliyyuna anya kuwa ba za ka koma Enugu cikin satin nan ba? Wallahi ji nake kamar mu dawwama tare". Ali ya yi murmushi ya ce"Hajiya kenan, na faɗa miki fa yadda wata shegiya ta gano ni, har ta so ta saka Maryam ta kama ni". Ta ce"To ai bayani za ka yi mata, ta duba alkhairan da kake samu a can". Ali ya yi murmushi ya ce"Hajiya kenan, ana ga yaƙi kina ga ƙura, ai tun da Maryam ta fara zargina gara na bar wannan layin kawai shi ne mafitata, kafin ta kama ni dumu-dumu na shiga uku". Hajiya ta ce"Ai shikenan, amma gobe ma za ka zo ko?" Ya ce"Sai dai jibi, kin ga yau zan yi lattin komawa gida, sai na harhaɗa ƙaryar da zan yi mata, idan gobe ma aka kuma haka za ta ramfo ni, amma fa ni ma ina kewarki Hajiyata, kin haɗa komai, ina mamakin wannan mijin naki da ya yi saken barin wannan garar". Ta yi murmushi ta ce"Aliyyu kenan!". Suka yi sallama ya tafi. Maryam tana zaune a falo ta ci kwalliyarta kamar ba dare ba, ta san yana hanya don haka har ta kawo abinci ta ajiye, tana kallo a wayarta tana duba lokaci, sai ga shigowar saƙo ta baƙuwar lamba, ta katse kallon ta shiga ta fara karantawa, _Ni Maryam yaushe zan zo ki ba ni sirrin riƙe miji? Ali yana shakkarki, shiyasa ya kasa sakewa da ni, ƙila kuma don ke amarya ce har yanzu,amm...ki ji ƙamshin turaren jikinsa idan ya yi miki daɗi ki faɗa min zan ba shi gobe ya kawo miki_. Tana fara karanta saƙon ta miƙe tsaye kamar an tsikareta, zuciyarta ta dinga tafasa tana jin kamar ta damƙo wacce ta rubuta saƙon ta cikin wayar, da sauri ta kira lambar ta ji ta a kashe, hannunta har rawa yake ta tura mata saƙon zagi har da masu gunna. Tana jin shigowar Ali ta yi wurgi da wayar kan kujera, ta fita da sauri har tana tuntuɓe, tun bai gama ajiye babur ɗinsa ba ta ce"Daga ina kake?" Ali ya yi murmushi ya ce"Maryama ta Ali, ai kya bari na shigo ɗakin ko?" "Ba shigowarka ce damuwata ba, kawai ka faɗa min daga ina kake?" Ta faɗa tana huci. Ya je ya rufe gidan, ya zo zai shiga ɗaki, ta janyo rigarsa ta dawo da shi baya tana sake cewa"Daga ina kake?" Sai kuma ta rirriƙe shi ta fara shinshina jikinsa kamar tsohuwar mayya, mamaki ya daskarar da Ali kawai yake binta da kallo, ita kuwa tana samun abin da take nema ta hankaɗa shi gefe ta shige ɗakin gado ta fashe da kuka, irin ƙamshin nan ne dai na wannan Hajiyar wacce ta zo gidanta, ƙamshin da ta sha jinsa a jikin Alin, don har kayan da ya kawo mata daga Enugu suna irin ƙamshin, da sauri Ali ya bi bayanta cike da mamaki ya shigo ɗakin, ta tashi zaune cikin ƙaraji ta ce"Kar ka ƙaraso!". Ali ya dakata a inda yake ya ce"Maryam lafiya? Ni anya ba ki da almatsutsai?" Ya ƙasara a tsorace. Ta yi masa mugun kallo kafin ta ce"Don Allah ka koma inda ka fito, ka kwana a can". Jikinsa ya fara yin sanyi abun ka da mara gaskiya, sai ya zauna a gefen gadon ya ce"Maryam daga ina na fito idan ba wurin aiki ba?" Ta ce"Ai saƙonta ya riga ka dawowa, kuma ƙamshin da yake tashi daga jikinka ya ƙarasa ba ni duk wani bayani da zan nema, Ali neman mata kake yi?" Ya ji maganarta ta ƙarshe kamar saukar aradu a kansa, ya kuma rasa abin da zai ce. Ta ce"Ka tabbatar mini mana, ka yi shiru! Yaushe ka fara? Har tsawon wane lokaci ka ɗauka kana linke ni?" Yanzu ma bai ce komai ba, ta sakko daga gadon ta nufi sif za ta fara kwaso kaya, ya zo ya riƙe hannunta, a fusace ta ce"Ka sake ni, don yau a gidanmu zan kwana! Ba zan taɓa iya zama da manemin mata ba sam!" Shi ma a fusacen ya ce"Maryam ya fa ishe ki haka! Kar ki sake jifana da waɗan nan kalaman, idan ba haka ba ranki zai yi mummunan ɓaci, kin sha ƙwaya ne da za ki dinga danganta ni da neman mata? Ko don kin ga ina ƙyale ki kina yadda kika so da ni? To wallahi ki shiga hankalinki, ko mene ne a kanki zan sauke miki shi!". Da mugun mamaki take zare idanu kamar za su zube a ƙasa tana nuna kanta ta ce"Ni? Ali ni kake faɗawa hakan?" Ya ɗan ji fargaba har zuciyarsa, amma ya dake ya ce"Na faɗa miki ɗin! A kan me za ki dinga zargina da mugun alkaba'ir?" Ta nemi waje a bakin gadon ta zauna, shi kuma ya fita ya koma falo, wayarta ya ɗauka a kan kujera, yana dubawa ya ga saƙon, ƙirjinsa ya buga da ƙarfi, ransa ya ɓaci, yanzu kam dole ya san Hajiya ce take son haɗa shi da matarsa, da sauri ya goge saƙon, ya ajiye wayar, ya nemi waje ya zauna zuciyarsa tana tafasa, ya ma rasa wane mataki ya kamata ya ɗauka, da wane idon zai kalli Maryam da ya san ta riga ta gama gane shi? Anya wannan hargagin borin kunyar zai kai shi kuwa? Ya zaunar da ita ya baje matsalar da ta afka shi a neman mata su samu maslaha shi da Maryam ko dai ya kafe akan sharri ake yi masa? Idan ya warware mata shin za ta fahimce shi ne ko dai za ta kai wa manya maganar? Idan iyayensu suka ji ya zai yi? Sannan yana fargabar ya rasa Maryam na har abada, wannan tunanin ne ya cunkushe masa ƙwaƙwalwa har ya saukar masa da ciwon kai, duk yadda wayarsa take ringin bai kulata ba, har bacci ya sace shi, ƙarfe ɗaya ya farka, ya miƙe daga kujerar yana murtsika ido, ya tashi ya je ɗakin gadon ya ga Maryam duƙunƙune a ƙarshen gado tana bacci, ya sauke ajiyar zuciya, ya koma falon ya zauna, ya ɗora daga inda ya tsaya a tunani, kafin ya janyo wayarsa ya fara duba miss call, akwai na Baby Farha har uku, da kuma wata lamba wacce har massage aka yi masa da ita, ya buɗe saƙon, ya fara dubawa, bayan sallama ake yi masa bayanin Dad ɗin Farha ne, ya kira shi bai ɗauka ba, yana son ganinsa gobe a gida ƙarfe goma na safe zuwa sha biyu, ƙirjin Ali ya doka da ƙarfi, ya mayar da amsa da cewar a yi haƙuri ba ya kusa da wayar ne, kuma zai shigo goben, ya sauke ajiyar zuciya yana kiran layin Farha, sai ya ji sa a kashe, "Allah ka fitar da ni!" Ya furta yana kwanciya, don bai shirya ƙara aure ba a halin yanzu, sannan ya san dole ya faɗawa Dad ɗin yana da aure, wanda bai san mene ne zai biyo bayan hakan ba, tun da Farha ba ta taɓa sani ba, shi dai a halin da yake ciki yanzu da za su ƙyale shi wallahi da sun taimaka masa, don dai kawai kar a ce masa mayaudari ne shiyasa zai daure ya je, shin ya ma Farha za ta yi idan ta san shi kafinta ne? "Cakwakiya" Ya faɗa yana lumshe ido. Washegari ya makara sallar asuba, don sai da gari ya yi haske tarwai ya tashi, ya yi alwala ya yi sallah, jin shiru bai ji motsinta ba, ya sa shi tunanin ko ita ma ta makara ne? Ya leƙa ɗakin, sai ya ga wayam babu alamarta, ga kuma sif ɗinta a buɗe da alamun an kwashi kaya, "Na shiga ukuna!" Ya faɗa a razane, sannan ya koma falo da sauri ya ɗauki wayarsa ya kira lambarta, har kira uku ba ta ɗauka ba, ya zauna jaɓar kamar zai yi kuka ya ce"Haba Maryam ya za ki yi min haka?" LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Ya bi ta da sauri yana cewa"Maryam, mu je a siyo tsiren nan don Allah, dama yunwa nake ji". Ta galla masa harara, ya bi ta da sauri ganin ta yi ɗakin gado, ya buɗe mata ƙofar, tana shiga ya shiga shi ma, ganin ta zauna a bakin gado sai ya fice ya tafi falo, ya haska su murya ƙasa-ƙasa ya ce"Hamza don ubanka ku fice mini daga gida, maza-maza!". Hamza ya miƙe yana cewa"Haba Ali mene ne haka?" Ali ya rage murya ya ce"Kai! Magana ake yi ta mutuwar aurena ta matso, ku fice kawai a hankali". Yarinyar tana kimtsawa Ali ya damƙi hannunta ya fice da ita kamar makaho da ɗan jagora, tana cewa"Kai meye haka ne?" Yana ƙara hankaɗa ta, Hamza yana ficewa Ali ya banke ƙofa ya rufe, yana juyowa ya ga Maryam tana haske-haske, a tsakar gida, ya ce"Lafiya me kike nema?" "Silifas ɗina" Ta faɗa ranta a ɓace. A tare gabansu ya faɗi ganin ta haska wasu takalma da ba na gidan ba, don buduruwar Hamza silifas ɗin Maryam ta saka, saboda fatattakar da Ali ya yi mata ba ta tsaya tantance nata ba, ta ce"Ali wannan takalmin fa na waye?" Ya yi shiru ya rasa ƙaryar da zai yi, sai kawai ya ciro waya daga aljihu ya kara a kunne yana cewa"Hello Alhaji, Aliyyu ne" Ya ɗagawa Maryam hannu alamar yana zuwa Zai fice ta janyo rigarsa ta ce"Babu inda za ka je, sai ka faɗa min takalmin wace shegiyar ce wannan?" Ali ya ce"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Wata ƙanwata ce fa ta zo wucewa ta ƙofar gidan nan, ta shigo don a zatonta kina nan, muka gaisa take ce min a ara mata silifas wai takaminta sai gurɗe ta yake yi tana faɗuwa, kuma ga goyo, abun dai akwai ban tausayi". Maryam da ko kalma ɗaya ba ta yarda da ita ba a cikin zancensa ta girgiza kai ta ce"Babu komai ka je ka yi duk yadda ka tsarawa kanka". Ya ce"Haba Maryam, wai me yasa kike yawan zargina ne? Wallahi da gaske nake, wata ƴar ƙanin babanmu ce, kin san yaran duk ba wani riƙe sunansu na yi ba..." Ta katse shi da faɗin"Wannan duk kai ta shafa, ni dai ka je ka samo min silifas". "Yanzu kuwa" Ya faɗa yana ficewa, ta bi shi da kallon tausayin kanta, har ma da shi ɗin, na wannan rayuwar da yake ƙoƙarin jefa kan shi a ciki. Babu jimawa ya dawo da sabon silifas, ta karɓa ta saka, kafin ta fito daga banɗaki ya fice sakamakon kiran Hajiya da ya shigo wayarsa, sun ɗan jima suna fira don wuri ya samu ya zauna, sai da suka gama ya wuce ya samowa Maryam tsire da lemo. "Kin ga na daɗe ko? Wurin ne da layi" Ya faɗa yana ajiye mata, ko kallonsa ba ta yi ba, ta ɗauki ledar ta je kitchen ta zubo a faranti, ta ci ta sha lemo ta bar masa sauran, ta je ta yi kwanciyarta, shi ma yana gama ci ya kashe wayarsa ya je ya kwanta, washegari suka tashi babu yabo, babu fallasa, hakan ya sa shi jin daɗi yana ayyana yanzu saura case ɗin Farha, da zai fita ta ce ya fice da takalman nan ko ta watsa su waje, ya saka su a leda salun-alun ya fice. GIDAN HARUNA Da duku-duku Baaba ta tashi ta yi wanka, har ta gama haɗa kayan Zainab cif bacci take ba ta farka ba, ta ɗaka mata duka ta tashi a firgice tana yamutse fuska, Baaba ta ce "Tashi ki wuce mu tafi". Da mamaki Zainab ta ce"Mu je ina Baaba? Wai dama da gaske kike?" Baaba ta ce"Na kai ki gidan ubanki mana, ai dama ba ki da inda ya fi can, na ɗakko ki don inganta tarbiyyarki to na ga sai dai ma ta ƙara taɓarɓarewa, idan kuwa haka ne ai babu wani amfani". Zainab ta fara matsar ƙwalla ta ce"Don Allah Baaba ki haƙuri, wallahi na daina har abada". Baaba ta ce"Kanki ake ji dai, idan ba za ki bi ni ba, fita na kulle ɗakin sai Harunan ya ba ki masauki, wallahi Zainab kun ci amanar Halima...." Sai ta fashe da kuka. Zainab ta tashi ta shirya suka ƙarasa tattara kayan, kayan sakawarsu dai duka suka kwashe, sai katifa da sauran abubuwa suka bari, Baaba ta ƙwanƙwasa ɗakin Haruna ya fito yana gaishe ta, ta tsuke fuska tana ƙirga kuɗi ta ce"Ungu wannan, jarin Halima ne na wake da shinkafa, sai ka kai mata, ka faɗa mata mun bar gidan, kai kuma ba zan ce Allah Ya yi maka abin da ka yi ba, tun da ƴaƴanka na Halima ne, ita kuma tana da kyakkyawar zuciya, sai dai na ce Allah Ya shiryeka!" Ya karɓi kuɗin, ya kalli Zainab da take kwashe masa ido tana ɗaga gira, mamakinta ya kama shi na ganin har yanzu ita ba ta saduda ba ashe, a zuciyarsa yake ayyana lallai wannan yarinyar tantiriya ce. Da daddare ya je gidansu Halima, suka gaisa babu yabo babu fallasa, ya yi shiru bai faɗa mata su Baaba sun tashi ba, don kar ta zargi wani abun, sati ɗaya yana zuwa gidan kullum sannan ya roƙi Umma kan Halima ta koma idan jikin nata ya yi sauƙi, don yanzun ba shi da wani abun ɗebe kewa, tun da Zainab suka tafi wayarta ba ta sake shiga ba, kuma an zo an kwashe duka kayansu, ta wani ɓangaren hakan daɗi ya yi masa, to sai dai matar da za ta tare a ɗakinsu Zainab ɗin yanzu mijinta matafiyi ne, yanzu haka ma ba ya nan ita kaɗai za ta tare, shi yasa ya so Haliman ta dawo, washegarin tanar Umma ta yiwa Halima nasiha kan ta dinga haƙuri shi laulayi ya gaji hakan dama, da kanta ta rakata har gidan, ta baro ta cike da ƙunci. Halima ta yi zaton Baaba unguwa suka je da ta ga ɗakin a rufe, haka ta zauna zuciyarta tana ta yi mata zafi, don dawowarta ɗakin sai take hango komai da ya faru a falon kamar yau ta gani, ta yi kuka ta share hawaye, dab da magriba Haruna ya dawo da cefane, ta yi girki, bayan sallar isha'i tana kwance ya shigo, ta yi kamar me bacci, tana ji ya gama abin da zai yi ya zo ya kwanta, a hankali ya kai hannunsa jikinta, wanda ta ji saukarsa tamkar wuta, ta tashi tana yi masa mugun kallo ta cikin duhun ɗakin, ya matso yana cewa"Halima mene ne haka?" Ta haɗiyi yawun baƙinciki ta ce"Yanzu Haruna da gaske har kana da sauran ƙwarin gwiwar kai ƙazamin hannunka jikina?" "Ni ne ƙazamin!?" Ya tambaye ta a fusace. Ta ce"Kai ne ƙazami! Ka ce ba za ka sake ni ba dai ko? Zan zauna da kai, amma ni da sake haɗa jiki da kai ba har abada!". Ransa a ɓace ya ce"Zama da ni ya zame miki dole, kuma tun da kina matsayin matata ina da ikon haɗa jiki da ke a duk lokacin da na ga dama, ko Allah muna yi masa laifi ya yafe mana, na ba ki haƙuri iya yadda zan iya, ki haƙura ko kar ki haƙura wannan zaɓinki ne!". Daga haka ya tashi ya fice, ya koma falo ya kwanta. Washegari sai ga matar da ta kama haya ta zo tarewa, Halima ta dinga mamaki, ta kira wayar Zainab don ta yi magana da Baaba, ta ji ta ƙi shiga, haka ta zubawa sarautar Allah ido, bayan ƴan'uwan sabuwar maƙociyar tata sun watse, ta shigo ɗakin Halima suka ƙara gaisawa sosai, yaranta biyu maza, kuma tana da ciki, take faɗa mata mijinta direba ne, me tafiye-tafiye, Halima ta saki jiki da ita, duk da tana jin damuwar rashin sanin dalilin tashin Baaba, babu sanarwa. GIDAN SADIQ Zaman Sadiq da Yusra ya zama babu yabo babu fallasa, duk wani haƙƙoƙin juna suna saukewa, amma sam babu sakin fuska da walwala, tsarin gidan ya koma kamar na baya, idan tana da aikin kwana sai dai ya dawo da wuri ya kula da su, wanda a yanzu yaran har so suke ta je aikin kwana, don a ranar Kursum ce take yi musu girki ya karɓo su ci, daga shi har yaran babu wanda bai ɗanɗana kewar girkinta ba, don da yara cewa suke ba za su ci abinci ba, su na Anti Kursum ya fi daɗi, sai da rana ɗaya Yusra ta haɗa su ta zane da bulala ta yi musu kyakkyawan gargaɗi kan idan ta sake jin sun ambaci Anti Kursum sai ta yanka su ta soya, sannan suka tsorata suka nutsu kuma suke cin abincin Yusra babu ƙorafi, sati biyu suna a haka, wata ranar Juma'a Sumayya ta zo mata da zancen ta ji labarin an saka ranar auren Kursum, maza ta bincika ta ji ko da mijinta ne, hankalin Yusra ya tashi, ranar aikin kwana ne da ita amma ba ta je ba, tana falo tana safa da marwa sai ga Sadiq ya shigo, ya san ba ta je aiki ba tun da ya je maƙota karɓo yaran aka ce masa suna gida, kallo ɗaya ya yi mata ya wuce ɗaki, ta bi bayansa, riƙe da ƙugu ta ce"Sadiq da gaske an saka ranar aurenka?" Ya ce"E jiya an saka wata huɗu har wannan da muke ciki, bayan babbar sallah in sha Allah!" "Da Kursum ɗin!?" Ta tambaya ranta yana ɗugunzuma. Cikin ko'inkula ya ce"Da ita ne". Yana shirin shiga banɗaki ta sha gabansa ta ce"Yanzu a wane matsayin nake?" "Uwar gidana, uwar ƴaƴana". Ya faɗa kai tsaye. Ta ce"Ina sharaɗinmu?" Ya ce"Wanne?" Ta ce"Na rabuwa da juna muddin za ka ƙara aure". Ya yi ƴar dariya ya ce"Wannan sharaɗinki ne ba nawa ba, to saboda haka ke ce mai amsar nan". Ta ce"Sadiq ka sake ni, don ba zan iya zama da kai ba". Ya ce"Ni kuma ban ga dalilin rabuwa da ke ba tukunna". A fusace ta ce"Ai kuwa za ka gani nan ba da jimawa ba". "Mu ga alkhairi" Ya faɗa yana shigewa banɗaki. Washegari da sassafe ta haɗa kayanta tsaf, tun kafin yaran su tafi makaranta, ta fito da akwatuna tana jiran yaronta Nura a falo, Sadiq yana ta kallonta bai ce komai ba, har yara suka tafi makaranta, sannan Nura ya zo ya fitar mata da kayan, ta yafa mayafinta ta ce"Sadiq za ka sake ni ne, ko za ka jira sammaci?" Ya ce"Zan jira sammacin dai". Ta gyaɗa kai ta fice, shi ma ya fita ya rufe gidan ya tafi shagonsa. Yaran suna dawowa daga makaranta ya zo ya ɗakko su a maƙota, ya shirya su, tare da kayan sakawarsu suka tafi gidan mahaifiyarsa, da mamaki Hajiya take kallonsa, kafin ta ce"Sadiq lafiya na ga yara da kaya?" Ya ce"E Hajiya, za su zauna ne kafin Yusra ta dawo". Nan ya kwashe komai ya faɗa mata, ranta ya ɓaci ta ce"To Sadiq ka sake ta mana! Me kake jira?" Ya girgiza kai ya ce"Hajiya ina ganin za ta sakko idan na ba ta iska, kin ga kowa da yanayin kishinsa, ni na san za ta haƙura daga baya, idan kuma ta dage sai na sawwaƙe mata, in sha Allah!". Hajiya ta ce"A to! A ce yarinya ta zaɓi aikinta fiye da aure, ta dinga wasarere da mijinta kuma ta ce a dawwama a haka kar ya auro wacce za ta kula da ita? Har ma ta samu ba a hana ta aikin ba, amma ta dinga cewa sai dai a sake ta, ai kuwa za a sake ta ɗin, don wannan auren dai ba zai fasu ba, zaɓi ya rage nata!". Kwanan Yusra uku a gida iyayenta suna ta tausarta, amma fir ta ƙi, ta kafe kan sai dai ya sake ta, sun kira Sadiq sun tattauna ya nuna musu ba zai yiwu ya fasa aure ba, saboda shi da yaran suna buƙatar cikakkiyar kulawa, kuma iyayen ba su ga laifinsa ba, sun yi mata nasihar duniya ta ƙi ɗauka, don haka suka kawo ido suka zuba mata, a ranar da ta kai Sadiq koto babu wanda ta faɗawa, sai da ta dawo, yana shago aka kai masa sammaci, ya ji babu daɗi sosai, don bai taɓa zaton za ta iya kai shi koton ba, ya yi niyyar sakinta idan har ta dage ta fi son rabuwar, ya rabu da ita ne kawai saboda yana tunanin za ta huce ko don yaranta. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 SADIQ Ana idar da sallar isha'i ya koma gida, ya yi wanka ya shirya ya tafi gidan su Yusra, sai dai ya samu labarin tana aikin kwana, don haka ta wuce asibitin kai tsaye, duk da bai saba hakan ba, a ƙofa ya tsaya ya kira ta a waya, ta ɗauka suka gaisa kamar babu wata a ƙasa, ya ce"Yusra na je gida ba kya nan..." "E ina wurin aiki" Ta tari numfashinsa. Ya ce"Na sani, yanzu ga ni a bakin asibitin zan iya ganinki?" Ba ta ce komai ba, ta katse kiran, ta fito ta same shi, tun daga nesa yake kallonta yana tuna tun farkon fara soyayyarsu, da yadda ta haukace akan son shi, ta ƙi kowa sai shi, hasali ma soyayyar ƙwatarta ta yi a wajen aminiyarta, shi kuma ya koyi sonta ne kawai saboda tsantsar kulawar da ta dinga nuna masa, da ma tausayin yadda ta kusa zaucewa a kan shi, amma wai yau shi take iya kai wa kotu saboda ya sake ta. "Sadiq" Ta faɗa don ta ga alamar ba shi da niyyar magana sai kallonta da yake yi. Ya sauke ajiyar zuciya ya ce"Yusra". Ta kalle shi ba ta ce komai ba, ya nisa ya ce"Na ga sammaci". Ta ce"E". Ya ce"Yanzu Yusra dama da gaske kike so na sake ki? Saboda zan ƙara aure za ki yanke wannan ɗanyen hukuncin? Na bar ki aikinki ban hana ki ba, me zai sa ni ki hana ni ƙara aure? Kin fi so ƴaƴanki su dawwama a haka suna yawon maƙota? Wace irin yarda kika yi wa maƙotan nan da har kike zaton nan gaba ba za ki yi danasani ba? Yaran nan fa mata ne, ƴaƴan gidan kuma duk maza ne manya da yara, sannan kuma ni ma lokuta da dama ina buƙatar kulawarki, amma haka zan haƙura saboda ba kya nan, ko sanda kike gidan ni lokacin kasuwata ne, ko kuma kin dawo a gajiye, duka na ɗaga miki ƙafa saboda na san kina son aikinki, idan kika duba ƙarin aurena kamar sauƙi ne a wurinki, idan yaranki suna gidana a zaune ke kanki sai hankalinki ya fi kwanciya, sannan kin san wacce zan aura kin san halinta..." Ta ɗaga masa hannu ta ce"Dakata haka Sadiq, don Allah ya isa, e tabbas na san Kursum, ita ɗin mayaudariya ce, ma ci amana, tantiriyar ƴar bariki, ko ba Kursum ba ni ɗin nan na fi ƙarfin na zauna na yi kishi da wata, ballantana mara class irin Kursum, ni babu wanda zai saka na canza ra'ayi saboda yarana, ba dai ka yarda da tarbiyyar wacce za ka aura ba? Ai ina ganin babu wata matsala ta wannan ɓangaren, sannan tun da ka iya tsallake ni ka so ta, ta fi ni komai, in sha Allah ko ka rabu da ni babu abin da za ka nema ka rasa, ni kuma na je na auri wanda zai iya bin tsarina". Ya ce"Rabuwar dai kika zaɓa har yanzu ko?" Ta ce"Har abada ma ita zan zaɓa Sadiq indai za ka ƙara aure". Ya ce"Shi kenan Yusra na gode, Allah Ya sa hakan ya zame mana alkhairi bakiɗaya, ni ba zan shiga kotu da ke ba, wannan zubarwa kanmu mutunci ne, saboda haka ki je idan kika gama idda ki yi aure". Daga haka zuciyarsa ta yi rauni, ya juya ya tafi, kai tsaye gida ya wuce, yana jin wani yanayi mara misali, a kujera ya kwanta, ya ɗauki wayarsa ya rubuta mata saƙo ya ce saki ɗaya yake nufi. Ita kuwa Yusra sam ba za ta ce ga ainahin abin da take ji ba, farinciki ko akasinsa, ta da san da gaske tana son rabuwa da shi, saboda haka yanzu tana jin burinta ya cika, ta ja ƙafa ta koma ciki, Sumayya da ke tsaye a gefe tana kallonsu ta zo ta tare ta tana cewa"Sister Yusra baƙo kika yi, na wuce na ganki da wani". Ta ce"A'a Sadiq ne". Ta ce"Ko dai za ki haƙura ki janye ƙarar ne?" Yusra ta sauke numfashi ta ce"Dama ai dole na janye, tun da ya saukewa kansa taurin kan da ya ɗauka". Da zumuɗin son jin asalin maganar Sumayya ta ce"Me kike nufi Yusra?" Yusra ta ce"Ya sawaƙe mini, ya ce idan na gama idda na yi aure". Sumayya ta sauke nannauyar ajiyar zuciya ta ce"Na taya ki murna Yusra, kin ga ko yanzu zancen ƙarin aurensa ya fito babu mai raina ki, an san sai da kuka rabu zai yi auren, kar ki wani saka damuwa a ranki, za ki samu wanda ya fi shi in sha Allah!". Yusra ta gyaɗa mata kai, ta ce"Bari na koma bakin aikina, sai mun haɗu". Sumayya ta saki makirin murmushi ta bi bayanta da wani kallo kafin ta ce"Yau burina ya cika, duk da dai na makara, ko banza na rama tun da na raba ku, kuma na raba ki da ƴaƴanki, ke da gidansa har abada, mayaudara maciya amana, in sha Allah ba za ki ƙara samun mijin da ya kai shi ba, kuma dole ki rayu da kishiya!". Ta yi huci mai zafi tunuwa da mawuyacin halin da ta shiga a baya sanadin soyayyar Sadiq, da yaudarar da ya yi mata, ta yi ƙwafa ta tafi harkarta. ALI Har ya manta da inda suka ajiye magana da gidan su Farha, sai rana ɗaya Daddy ya kira shi a waya, suka gaisa ya ce"Aliyyu ya mun yi da kai za ka dawo idan ka yi shawara kuma na ji ka shiru har yau?" Ali ya ce"Ai Daddy shawarar ce da aka yanke na san ba lallai ta yi maka daɗi ba, kuma da na ga Farha ma ta faɗa min kar na sake kiranta ko a waya ne, don aurenmu ba zai yiwu ba shi yasa kawai na tattara komai na ajiye ban sake nemanka ba". Daddy ya ajiye numfashi ya ce"Duk da haka ina son ganinka Aliyyu, amma ka ba ni adress ɗin gidanka, ni zan zo, don ba na so Farha ta san mun haɗu". Ali ya yi jimm, sannan ya ce"Ok zan turo maka". Ya tura masa yana ta tunanin dalilin da zai sa Daddyn ya zo har gidansa. Kwana biyu tsakani sai ga kiran Daddy da yamma, ya ce masa yau zai zo, don haka Ali ya dawo da wuri daga wurin aiki, sai dai fargaba ta hana shi faɗawa Maryam zai yi baƙo, gani yake kamar za ta gano dalilin zuwan baƙon, ya yi sa'a ma ba ta tambaye shi dalilin dawowarsa da wuri ba. Ƙarfe biyar Ali ya ji tsayuwar mota har ƙofar gidansa, wayarsa tana ƙara gabansa ya faɗi, yana dubawa ya ga shi ɗin ne kamar yadda ya yi zato, yana ɗagawa ya faɗa masa ya ƙaraso, ya kalli Maryam ya ce"Kin ga dama akwai wani baƙo da zan yi, ki ɗan shiga ɗakin gado za mu shigo". Ba ta ce komai ba, ta tashi ta bar falon, Ali ya fita, Daddy ya buɗe masa ƙofar motar ya ce"Malam Ali bismillah!". Ali ya shiga yana gaishe shi tare da ɗan sunkuyar da kai, sannan ya ce"Daddy mu shiga daga cikin gidan". Daddy ya girgiza kai ya ce"A'a Aliyyu na gode, yanzu dai ka fita ka buɗe bayan motar nan akwai kaya ka shiga da su ciki naka ne". Ali ya ce"A Daddy kaya kuma?" Ya gyaɗa masa kai yana duba wayarsa. Ali ya fita, yana buɗe bayan mota ya gan shi maƙare da kayan abinci, buhun shinkafa, taliya, macaroni, couscous, indimei, kayan shayi mai ma galan uku ne, har da su maggi, da sauran abubuwa, jikinsa ya yi sanyi, ya dawo ya ce"Amma Daddy..." Daddy ya girgiza kai ya ce"Kar na ji komai, azumi ne yake gabatowa dama na saba kyautar kayan abinci, don haka ka shiga da su kawai". Ya ce"To na gode Allah Ya ƙara arziƙi, Allah Ya saka a mizani". Sannan ya fara lodar kaya yana shiga da su, sanda ya kai na ƙarshe ya ce"Maryam ki duba ki ga abun arziƙi, wani Alhaji ne ya kawo min sadakar azumi har gida!". Maryam ta yi masa kallon sheƙeƙe ta ce"Alhaji ko dai Hajiya?" Ya ce"Kai ke kam kin gamu da aiki, ina zuwa" Ya fice, ta tasho ta saka hijjabi ta leƙa kaɗan, ta ga mota amma ba ta hango na ciki saboda duhun glass ɗin motar, ta tsaya duk da haka tana fatan na ciki ya fito. Ali zai ci gaba da godiya bayan ya zauna a motar Daddy ya ce"Ali ya isa haka, ba cika son godiya ta yi tsayi ba, komai don Allah muke yi". Ali ya jinjina kai, yana ayyana kirkin Daddy. Daddy ya ce"Ali na ji maganar Farha ta watse, tun da babu wanda zai yi mata auren dole, to sai dai kuma ni ba na so na lasawa mutum zuma a baki na janye, a baya na yi maka alƙawarin baka gurbi a shagon kasuwa, to zan baka in sha Allah ko babu alaƙarku da Farha ni na yaba da hankalinka". Ali ya ji farinciki sosai, ya ce"Ma sha Allah Daddy, na gode sosai". Daddy ya ce"A wannan babu komai Aliyyu, gobe da safe zan aiko a ɗauke ka idan ka shirya, za a kai ka kasuwa a nuna maka komai, in sha Allah za ka samu alkhairi fiye da sana'ar kafinta da kake yi". Ali ya ce"Allah Ya saka da alkhairi, Daddy Allah Ya ƙara girma". Daddy ya ce"Yawwa ni zan wuce, a gai da Madam ɗin". Ali ya fita, ya rufe masa motar, har Daddy ya kunna motar sai ga Maryam ta fito kamar an jefota, tana cewa"Ɗan dakata!". Daddy ya kashe motar yana kallonta, tana ƙarasowa ya zuge glass, duk a zatonta mace za ta gani, ganin dai da gaske Alhajin ne ta wayance ta ce"Alhaji ina wuni? Dama godiya na zo, Allah Ya saka da alkhairi". Daddy ya washe baki ya ce"A babu komai Madam, ni ma na gode". Ya kashe mata ido kafin ya zuge glass ɗin, wanda ya sa ta jin faɗuwar gaba. Ya ja motar ya tafi, yana cewa"Kyakkyawar yarinya". Ali da fara'ar fuskarta ta ɗauke ya ce"To ko ki bi shi ki yi bincike, ko ki wuce mu shiga ciki". Suka shiga, jikinta duk ya yi sanyi, ta ce"Wane ne wannan mutumin, a ina ka samo shi?" Ali ya ce"Wallahi wannan shi ne ya yi mana hanyar zuwa Enugu, to dama ya duba ƙwazon wasu daga cikinmu ya karɓi lambarmu ya ce zai neme mu, kin ga sai yau ya tuna da mu, ya kawo mana kayan azumi, yanzu haka kuma zai sama mini gurbi a shagon kasuwa, gobe ma zan fara zuwa in sha Allah!". Maryam duk sai ta yarda da shi, ta ce"To Allah Ya tabbatar mana da alkhairi". Ya amsa da amin, suka shiga duba kaya. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 SADIQ A sanyaye ya shiga gidansu, ya tari yaransa da suka rugo da gudu wurinsa, ya rungume su cike da tausayin sabuwar rayuwar da take tunkaro su ta nesa da mahaifiyarsu, zama ya yi shiru bayan sun gaisa da Hajiya, ta kalle shi ba ta ce komai ba, ta san yana son Yusra dole ya shiga damuwa idan ta yi nesa da shi, can dai ya sauke ajiyar zuciya ya ce"Hajiya ban san da ya za ki kalli maganar da zan faɗa miki ba". Hajiya ta ce"To mene ne kuma yake faruwa?" Sadiq ya ce"Yusra ta kai ni ƙara kotu, an kawo mini sammaci, saboda tana neman saki daga wurina, ni kuma sai na ga ba zan bari ta kai mu ga haka ba, saboda haka jiya da daddare na je na same ta mun tattauna, na lura hankalinta ya tafi kan a rabun kawai, shi ne na sake ta, na yi mata saki ɗaya, wanda kuma ba ni da niyyar kome sai idan ita ce ta nema". Hajiya ta ce"Ikon Allah! Ai dama shi aure rai ne da shi, Allah Ya sa hakan ya zame muku alkairi baki ɗaya". Ya amsa da amin, yana tashi zai tafi, Hajiya ta ce"Sadiq zauna". Ya dawo ya zauna, ta ce"Tun da dai kun rabu da Yusra me zai hana a rage saka ranar aurenka? Tun da dama kana tunanin inda za ka ajiye ta ne, yanzu kuma ga wuri, sannan bai kamata ka yi ta zama babu mata ba". Ya ce"To ai Hajiya ba lallai ita ɗin gidansu sun gama shirinsu ba, zan tuntuɓa na ji, indai babu matsala sai a rage ɗin". "Yawwa ka tuntuɓa mu ji, ni idan son samu ne ma a yi kafin azumi wallahi" Hajiya ta faɗa cikin tausayawa ɗanta. Suka yi sallama ya tafi. Washegari da safe sai da Yusra ta gama baccinta, ta yi wanka ta karya sannan ta sanarwa mahaifiyarta mutuwar aurenta, ta ce mata Allah Ya sa hakan shi ya fi alkairi, sannan ta shirya ta koma kotu ta janye ƙara, kuma a ranar aka kwashe duka kayanta daga gidan Sadiq, don ta saka a ranta ita da shi sun yi hannun riga. Da Sadiq ya yiwa Kursum magana a kan yiwuwar rage ranar auren ta ce za ta faɗa a gida ta ji, to dayake dama duk wata shawara da Sumayya ake yi, ita ta ce babu matsala a bar shi a duk lokacin da ya ce, tun da dama ita ce ta yi alƙawarin yi mata kayan ɗaki tun da aka saka ranar, kayan kitchen kuma dama Kursum ta haɗa abunta, sai ƙananun abubuwan da ba a ƙarasa ba, saboda haka babu wani ɓata lokaci aka matso da ranar auren za a yi kafin a fara azumi, kuma a ranar Sumayya ta faɗawa Yusra ta ce mata ita ma a gari ta ji, ta haɗa da nuna mata gara da ta rabu da Sadiq domin hakan da ya yi ya nuna dama can ya gaji da zama da ita, ga shi daga rabuwarsu ya matso da ranar aurensa, Yusra ta gamsu da hakan, ta sake jinjina butulcin namiji, ta ayyana dama ashe wata ƙaya ta zamewa rayuwarsa yanzu ya cire ya huta, saboda haka ta ƙudurce a ranta tana gama idda ita ma za ta yi wani auren. Bayan sati uku aka ɗaura auren Kursum da Sadiq, sai ranar auren Yusra ta sake jin zafin cin amanar da Kursum ta yi mata, babban abin da ya ɓata ranta bai wuce yadda maganar ta yaɗu a asibitinsu ba, ana ta cewa Yusra lusara ce da har ta yi saken da ƴar aikinta ta ƙwace mata miji da ƴaƴa, don har ji ta yi ana cewa dama yaran tuntuni suka zaɓi Kursum ɗin fiye da Yusra, har da batun girki ma mijin da yaran duk sun shaida nata ya fi na Yusra, don haka yaran ma murna suke yi da mutuwar auren, mutane da yawa sun tare da zancen, wasu su yi ta zuga ta wai ta ɗauki fansa a kan Kursum, wasu su nuna mata ba komai ba ne, za ta samu wanda ya fi shi, haka ta dinga gani ana yi mata habaici a status, har zancen ta kai Sadiq kotu sai da ya fito, da kuma cewar har asibiti ya biyo ta ya ci mata mutunci sannan ya saketa, a ranar Yusra kasa zaman asibitin ta yi, ta koma gida ta shiga ɗaki ta dinga kuka, ta rasa ta ina za ta ji sauƙi, don ta ma kashe wayarta saboda masu kiranta suna yi mata zancen shirme, mahaifiyarta kuma ta ƙi kulata, saboda tana tunanin kishi ne yake ɗawainiya da ita. A iya saninta bayan Sumayya babu wanda ya san wasu abubuwan da ya shafi auren nan, sai dai wani sashe na zuciyarta yana faɗa mata Sumayya ba za tozarta ta ba, duk da tana ƙarfafa zargi a kanta, tun da indai ba Sadiq ne yake faɗawa Kursum komai ba take bazawa a gari, ba ta ga ta inda maganar za ta fita ba, kuma ta san Sadiq ba shi da wannan halin na surutu barkatai, duk da ba ta sani ba ko giyayyar soyayya ta makar da shi ya fara. Washegari da safe ba ta fita aiki ba, ta yi mamaki da Sumayya ba ta kira ta ta ji dalili ba, tun da ta saba da hakan, da azhar ita sai ta kira ta, suka gaisa take cewa"Sumayya kin ga ban je aiki ba shi ne ko ki bincika ki ji ko?" Sumayya ta ce"Oh ba ki je ba? Dayake ni ma ban je ba fa, da sauran gajiyar jiya a jikina, amma tun da an gama taro mun kai amarya ɗakinta gobe zan shigo in sha Allah!" Da ɗan mamaki Yusra ta ce"Au Sumayya biki kuka yi?" Ta ce"E mana, bikin Kursum ƴar ɗakina mana, na san ko na gayyace ki ba lallai ki zo ba, kin san ni ce na yi komai na sha'anin bikin, sai da na ga ta shiga ɗakin Sadiq sannan hankalina ya kwanta". Yusra ta miƙe tsaye a razane ta ce"Sumayya me kike faɗa haka? Kina magagin bacci ne?" Ɗiff Sumayya ta kashe wayar ba tare da ta ce komai ba, zuciyar Yusra kamar za ta fashe don azalzala mamaki ya cushe mata kai, har ta rasa wane tunanin za ta yi ma, hijjabi kawai ta saka ta ɗauki wayarta ta fice zuwa gidan Sumayya, dayake babu nisa tsakaninsu a ƙafa ta je, tana zuwa ta banka ƙofar gidan ta shiga, Sumayya ta fito tana yi mata kallon tara saura kwata ta ce"Ke kuma haukan da ake ta faɗa a gari kin fara ya tabbata kenan! Ya za ki shigo min gida ko sallama babu?" Yusra ta ce"Da gaske!? Sumayya da gaske ni kike cewa mahaukaciya? Me kike faɗa mini a waya, sam ban fahimta ba!". Sumayya ta ce"Ta ya za ki fahimta tun da ke kanki ba ya ja? Ke a naki daƙiƙin tunanin zan manta irin yaudarar da kuka yi mini ke da Sadiq? A zatonki na yafe miki? To tun daga ranar da Sadiq ya aure ki nake jinya a cikin zuciyata, sai ranar da ya sake ki na warke tass, na yi shekaru da burin ganin aurenku ya mutu ko kuma ya tarwatse ku kasa zama lafiya, duk da a yanzu babu sauran soyayyar Sadiq a zuciyata amma ina baƙincikin na buɗe ido na ganku tare a inuwar ma'aurata cikin nishaɗi, ko Sadiq ya mayar da ke ɗakinki a yau Alhamdulillah, tun da na yi nasarar sanadin tsinke igiya ɗaya a tsakaninku, ballanta ma karatun da na yi wa Kursum ta haddace ko kin koma gidan Sadiq in sha Alla babu wani abu da za ki tsinta sai tarin baƙinciki". Daga haka ta juya za ta koma ɗaki, Yusra da ta daskare sai hawaye da yake gudana a idanunta, ta yi ƙarfin halin faɗin"Na gode da komai Sumayya!". Ta juya za ta tafi, Sumayya ta ce"Yusra kin yi mini, na rama, tun da mai faruwa ta faru komai ya wuce, yanzu sai mu koma kamar da, babu wani ƙulli a tsakaninmu, kar ki manta ba mu da abokan shawara sai junanmu". Yusra ta fice daga gidan, tana gani dishi-dishi, saboda ruwan hawayen da ta kasa tsayarwa, tana shiga gidansu ta wuce ɗaki ta kwanta, sai a yanzu take jin da gaske ita wawiya ce, ba ta taɓa zaton Sumayya ba ta yafe mata ba sai a yau da ta faɗa mata, tana ta mamakin wace irin mummunar zuciya ce da Sumayya da take ta ruƙonta har tsawon shekaru shida? Ta saka a ranta tun da ta bar Sadiq ta bar shi kenan har abada, aure yana da rai, ko Sumayya ba ta yi haka ba Allah Ya ƙaddara iya zamansu kenan, saboda haka babu buƙatar ta yi masa bayani, wanda hakan zubarwa da kanta mutunci ne kawai, sai dai gefe guda tana tunanin wace irin zuciya ce da Kursum, kuma son tsakani da Allah take yi wa yaranta? Sai a yau ta ji rashin kyautawarta na zaɓin rabuwarta da Sadiq saboda yanzu ta fara tuna yadda rayuwar yaran za ta kasance. ALI Washegari da safe ya shirya tsaf, yana zaune suna taɓa fira da Maryam kira ya shigo wayarsa, bayan ya ɗaga aka faɗa mata ya fito Alhaji ne ya aiko a tafi da shi, Ali ya tashi ya yi wa Maryam sallama ya fice, mota ya shiga suka tafi. Babban shago ne aka kai shi, na siyar da kayan siyarwa kala-kala na maza da mata, kuma ya yi mamaki da kai tsaye aka ɗora shi a matsayin cashier, ba tare da sanin halinsa ba, ya san dai Daddy ya yarda da shi ne kawai, don haka ya saka a ransa zai riƙe amana. Satinsa uku da fara zuwa aiki, aka fara azumi, a ranar azumin farko ne kuma Daddy ya nemi Ali ya zo gidansa shan ruwa, ya tafi yana jinjina kirkin Daddy, a ɗakin baƙi suka sha ruwa tare yana ta jansa da fira, bayan sun gama ya ce"Aliyyu akwai dalilin da ya sa na kira ka gidana yau". Ali ya ce"To Daddy ina sauraronka". Ya ce"Aliyyu wannan tambayar da zan yi maka tsakaninmu ne mu biyu, ina so ka amsa mini ita kana kallona a matsayin abokinka ba Daddy ba". Ali ya fara jin fargaba, duk da a iya saninsa bai yi laifin komai ba, ya ce"To Allah Ya ba ni ikon amsawa". Daddy ya ce"Aliyyu na san Farha, yarinya ce mara kamun kai, ta lalata rayuwarta sakamakon rayuwar ƙarya da kuma burin auren wani mai kuɗi da ta saka a ranta, abun ya kai duk wai wanda ya yi soyayya da ita abu ne mai sauƙi ta ba shi jikinta, na san ba ka da kuɗi, amma za ta iya yarda da kai saboda son da take yi maka, tambayar a nan shi ne, Aliyyu tsakaninka da Allah a soyayyarku da Farha kun taɓa samun irin wannan kusancin?" Ali ya yi saurin girgiza kai ya ce"Wallahi tallahi Daddy ko hannunta ban taɓa riƙewa ba, babu wata alaƙa da ta haɗa mu sai ta soyayyar fatar baki". Daddy ya ce"Na yarda da kai Aliyyu, saboda na yarda da gaskiyarka, to sai dai ina neman alfarma guda ɗaya a wurinka, wacce idan ka yi mini ita zan yi ƙoƙarin ɗaga darajarka zuwa inda ba ka yi zato ba, za ka samu kuɗin da ba ka taɓa mafarkin kama su ba". Tuni fargaba ta shige shi, ya ce"Daddy amma wannan wace irin alfarma ce?" Daddy ya ce"A yanzu haka Farha tana da ciki, kuma sai jiya ta san da zamansa a jikinta, yayarta ba ta kai ga sani ba, haka ita ma Farha ina tunanin ba ta kai ga tantance ko cikin wane ne ba, saboda haka nan ba da jimawa ba ina so ka amsa cewar cikin jikinta naka ne!". Ali ya ɗago da sauri ya yi masa wani kallo mai wuyar fassara kafin ya ce"Daddy! Me kake nufi da ni? Me yasa ba za a nemi wanda ya yi mata ba? Kuma me yasa sai ni za ka nema, duk cikin yaranka? Ni da ba ka daɗe da sani na ba?" Daddy ya ce"Saboda kai na so da alkhairi..." Da sauri Ali ya katse shi yana tashi tsaye ya ce"A'a sam ba ka so ni da alkairi ba, ban taɓa riƙe hannun Farha ba, saboda haka babu dalilin da zai sa na karɓi cikin jikinta hat abada!" Daga haka ya fice daga ɗakin, ya bar gidan zuciyarsa tana ta tafasa, sai yanzu ya fahimci dalilin da ya sa Daddy yake jansa a jiki duk da sun rabu da Farha, da ƙunar rai ya ƙarasa gida, yana jin kamar zai kama da wuta. Duk yadda ya so daidaita yanayinsa kar Maryam ta gane ya kasa, haka ya shiga yana haki, sai dai yana shiga ya tarar da ita tana hawaye, da mamaki ya ce"Maryam mene ne? Ba ki da lafiya ne?" Ta gyaɗa masa kai alamar e, ya ce"Kuma mene ne na kukan? Me yake damunki?" Ta ce"Ciwon kai ne, na sha magani amma" Daga haka ta tashi tafita, wayarta riƙe tamau a hannunta, banɗaki ta shiga, har da saka sakata, ta shiga goge saƙonnin da aka turo mata yanzu, tun sati uku da suka wuce ta tsinci kanta a wannan halin, da farko ta whatsApp wata lamba ta yi mata magana, wai wani ne ya ganta yake sonta, ta faɗa masa tana da aure ta yi block lambar a lokacin, daga nan ya canza lamba yake yi mata bayanin ya san tana da aure, shi ma ba wai ya ce aurenta zai yi ba, jikinta yake so idan da dama zai biya ta duk kuɗin da ta yanke, sosai hankalinta ya tashi sanda ta yi arba da bidiyoyin da ya turo mata, ta goge ta sake block ɗinsa, daga nan fa kullum ta kunna data sai ta ga irin saƙon da sabuwar lamba, ƙarshe sai ta haƙura ta goge whatsApp ɗin duka, sai aka koma kiranta a waya, tana jin shi ne sai ta kashe, ta saka a blacklist, haka saƙonni babu dare babu rana, ta kasa faɗawa kowa saboda tana ganin ba lallai Ali ya yarda da ita ba, duk ta shiga damuwa, akwai ranar da Ali bai daɗe da fita ba aka ƙwanƙwasa ƙofar gidanta, tana buɗewa ta ga wani matashi ne a kan babur, ya miƙo mata leda ya ce ga shi in ji wani, tana karɓa kafin ma ta duba ya buga babur ya tafi, tana buɗewa ta ga condom ne da yawa a ciki, hankalint ya tashi, har ta saka a shara sai kuma ta ɗakko ta kai shi ɗaki ta ɓoye a sif da zimmar idan ta fita unguwa sai ta zubar a hanya, to yau kuma saƙonnin da yake yi mata faɗa mata yake ko dai ta yarda da shi, ko a yau ya turo a kashe mijinta, kuma har lokacin ba ta jin za ta iya faɗawa Ali halin da ake ciki. Sai da ta wanke fuskarta ta fito, ta ɗakko abinci ta kawo masa, shi ma yana zaune jugum ya yi nisa a duniyar tunani, ta ajiye ta zauna ta zuba masa, ya ce"Maryam a ƙoshe nake fa, na sha ruwa a waje, ke kin ci?" Ta gyaɗa masa kai ba don ta ci ɗin ba, sai don ba ta da nutsuwar cin, tunani take yi ba ta san wane ne wannan mutumin ba, ba ta sani ba ko da gaske zai iya aikata abin da ya ce, saboda haka ta kalli Ali cikin tausayawa ta ce"Ali yau bai kamata mu kwana a gidan nan ba, ka tafi gidanku ka kwana, ni ma zan tafi gidanmu". Da mamaki ya kalle ta kafin ya ce"Maryam, wannan wace irin magana ce? Me kike nufi?" Ta ce"Jikina yan ba ni wani abu mara kyau zai iya faruwa, don Allah mu yi yadda na ce kawai". Ali ya ce"Maryam a kwana biyun nan na lura ba ki da nutsuwa, ni ina tunanin akwai abin da yake damunki, gobe zan kai ki gida ki huta in sha Allah!". Ta ce"A'a, yau ba za mu kwana a gidan nan ba, akwai matsala!". Ya ce"Babu wata matsala in sha Allah, ki daina yarda mummunan tunani yana yin tasiri a zuciyarki, ki dinga yin addu'a babu abin da zai same ki in sha Allah!". Ta gyaɗa masa kai ba don ta gamsu ba, sannan ta je da kanta ta saka sakata a gidan, ta dawo ta ci abincin kaɗan, ta sha ruwa, sai ta tsinci kanta da son kwanciya a jikinsa, ta yi matsashi da ƙafafunsa, shi kuma ya shiga shafa kanta ba don hankalinsa yana wajenta ba. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN ALI Sun daɗe a haka, kafin ya ce"Maryam akwai abin da yake damunki ne?" Ta yi shiru don ba ta son faɗa masa, ya ce"Na lura kina da damuwa, kwana biyu har tsiwarki ta yi sauƙi, hakan kuma ba ya yi mini daɗi sam, don Allah idan wani abun ne ki faɗa mini". "Babu komai" Ta faɗa tana riƙe hannunsa, suka yi shiru na ɗan lokaci kafin ta ce"Mu je mu kwanta, bacci nake ji, kuma ka ga za mu tashi sahur". Ya ce"Kin ga kuwa ina da niyyar siyo biredi ma, ga shi na sha'afa, bari na je na samo". Ta girgiza kai da sauri ta ce"Don Allah kar ka fita, ga abinci nan, dama ba na kirki muka ci ba, sai na ɗumama da asubar". Bai ce komai ba, suka fito ya rufe falon, suka shiga ɗaki ta saka sakata, suka kwanta shiru, kowa da abin da yake saƙawa a ransa, tana jin lokacin da ya yi bacci, ita kuwa baccin ya ƙaurace mata, fargaba kawai take ta abin da zai iya faruwa a daren, don har zuciyarta ta yarda da gaske wannan ɗan iskan mutumin zai zo ya yi abin da ya ce, ta so ta rage tsayin daren da nafila, sai dai tsoron fita yin alwalar ya hana ta, haka ta dinga saƙa da warwara a zuciyarta, sai wajen ƙarfe uku bacci mai nauyi ya kwashe ta, alarm ɗin wayarta yana bugawa Ali ya kashe, ya haskata ya ga bacci take yi sosai, shi ya fita ya kunna wuta ya ɗumama abincin, ya dafa shayi, sannan ya tashe ta, ta tashi a firgice tana kiran sunan shi, har abun ya ba shi mamaki, ya ce"Lokacin sahur ya yi fa, kar mu makara". Ta sauke ajiyar zuciya, tana mamakin yadda aka yi bacci ya yaudareta, ita da ta ƙudure a ranta yau ɗin ba za ta yi bacci ba, ashe da wani abun ya faru ma sai an gama za ta farka, bayan sun gama sahur ita zama ta yi tana istigfari, don kokowa da baccin da yake fizgarta, ba ta son kwanciya sai ta yi sallah, yayinda shi kuma ya ɗauki wayarsa yana chart, har aka kira sallah, ya tafi masallaci ita kuma tana idar da sallah ta kwanta, sai yanzun ne take baccin da nutsuwa. Washegari da safe sai da ya fita ta kunna wayarta, don yanzu haka take ba ta barin waya a kunne idan yana gida, da saƙon mutumin ta fara cin karo, ko karantawa ba ta yi ba, ta goge ta ajiye wayar. Shi kuma yana zuwa wurin aiki ya samu labarin an sallame shi daga yau, bai yi wani mamaki ba, ya kira lambar Daddy bayan ya fito daga wurin, suka gaisa kamar komai bai faru ba, Ali ya ce"Daddy yau na shigo aiki aka ce an sallame ni". Daddy ya ce"E, idan kana son ci gaba da aikinka ka zo gida mu ƙarasa maganar jiya". Ali ya yi guntun murmushi mai sauti ya ce"Ba ni da alaƙa da maganar jiya, na watsar da ita a inda aka yi ta har abada, indai saboda ka yi amfani da ni don cim ma wata manufarka ka janyo ni jikinka, Allah Ya yi mini sakayya, na haƙura da aikin, kafin ka ba ni aikinka ba a mace ka gan ni ba, saboda haka rasa aikinka ba zai kawo ƙarshen rayuwata ba". Bai jira cewarsa ba, ya kashe kiran, ya koma gida jikinsa a sanyaye, ya tarar da Maryam a kwance, ya saki fuska yana cewa"Azumin ne ya fara taɓa ki tun yanzu?" Ta ce"Ya na ga ka dawo?" Ya ce"E, yau hutu ake yi a shagon". Ta fita ta fara wanke-wanke, ya zauna yana yi mata ɗaurawa suna ɗan taɓa fira. GIDAN HARUNA Sosai shaƙuwa ta shiga tsakanin Halima da sabuwar maƙociyarta maman Usman, a yanzu har ta haƙura ta daina kewar Baaba, don daga lokacin ba ta sake jin labarinsu ba, ta tambayi Haruna ya ce shi ma gani ya yi kawai suna kwashe kaya, ga shi ta kira lambar Zainab layin ba ya tafiya, ba ta san gidan ko wani nasu ba, ga shi ba ta san yadda aka yi mata da jarinta ba, don Haruna bai ma faɗa mata an ba shi ba, ballantana ya bata kuɗinta, a yanzu laulayin ya fara sauƙi, sai dai wani irin zama suke yi da Haruna, rayuwar da yake yi da ita tamkar an zare masa tausayinta, yanzu abincin ma sai ya ga dama yake bata, sa'arta ɗaya kullum idan maman Usman ta yi girki sai ta ciko mata kwano, kuma abincinta lafiyayye, wataran har na safe ita ce take bata, ranar da ba ta bata ba kuma ta zauna a haka, kuma mace ce mai ilimin addini, don ita da kanta ta nemi Haliman ta zo su dinga karatu, haka kuwa aka yi, kullum da daddare bayan magriba sai ta ɗorawa Halima karatun Qur'an da hadisi. A yanzu babban takaicinta bai wuce yadda yake karɓar hakkinsa ta ƙarfin tuwo ba, ya riga ya dasa mata tsanarsa ya cire mata sha'awar mu'amular auren gabaɗaya, ba ta jin za ta sake jin daɗin haɗa shimfiɗa da shi har abada, saboda haka babban baƙincikinta shi ne ya taɓa jikinta, kullum sai ta zubar da hawaye, idan ta tuna yadda ta gan shi da Zainab, hoton ya ƙi barin kanta, ga shi ko kunya ba ya ji ya hana ta abinci kuma da daddare ya ce zai zo gare ta, ta koma gida har sau biyu mahaifiyarta tana dawo da ita, tun maman Usman tana kau da kai da shiga lamarinsu har watarana ta yi mata magana, ta ce"Halima wace irin rayuwa kuke yi da mijinki ne? Me yasa yawanci da daddare nake jiyo ku? Hakan babu daɗi, ga ki da ƙaramin ciki ke da za ki dinga lallaɓa jikinki amma har ki bari kuna irin haka ana jiyo motsi da hayaniyaku? Me yasa ba za ki ba shi haƙƙinsa ba? Kodayake samu ma kika yi, ni da mijin ma ba mazauni ba ina na samu ma ballantana ya yi min yawan da zan yi rowa?" Halima ta yi murmushin takaici ta ce"Maman Usman ban so kika shiga maganar nan ba, kin ganmu ne kawai muna rayuwa, ba ki san wane ne Haruna ba, da a ce kin san shi ƙila da ba ki ga laifina ba, a hakan ma na jure iya yadda zan iya" Sai hawaye ya zubo mata. Maman Usman ta ce"Mai ɗaki shi ya san inda yake yi masa yoyo, ni ma na san bai kamata na shiga wannan maganar ba, sai dai ina kallonki ne kamar ƙanwata ta jini Halima, shi yasa na yi zaton ko zan iya jin matsalarki na duba yiwuwar sama miki maslaha, idan abun ya fi ƙarfina sai na taya ki da addu'a". Halima ta ce"Na sani, kuma na gode Allah Ya bar zumunci, sai dai wata maganar babu amfanin tada ita, Allah Yana kallon kowa, kuma akwai ranar hisabi". Daga haka suka bar firar, tun daga nan sai Halima take jin nauyin a ce dare ya yi Maman Usman ta jiyo ta, sai ta ƙyale Haruna ya yi yadda ya so, zuciyarta na ƙuna. A ranar da aka ɗauki azumin farko Halima ta shiga sabon tashin hankali, sakamakon zuwan Zainab gidan da wasu mace da namiji wai ana neman Haruna, aka yi sa'a yana nan, don da sassafe ne suka zo, ya fita suka tsaya a zaure, amma su Halima da ke cikin gida suna jiyo tattaunarwasu, saboda babu mai sassauta murya a cikinsu idan ba Haruna ba, sai Zainab da take kuka, da farko ba ta san a kan me akan maganar ba, har sai da aka fara hayaniya macen tana cewa"Ai fa babu wata hujjar kare kanka da za ka kawo, tun da har Baaba ma ta shaida ta kama ku har sau biyu, ta tabbata ciki naka ne!". A zabure Halima ta miƙe tsaye daidai lokacin da ta ji wannan furucin, zuciyarta ta dinga bugawa da sauri-sauri, ta ɗora hannu a kai tana jin kamar ta kurma ihu, kuma ta yi shiru dai, tana jiyo muryar Zainab tana cewa"Ni tun da muka dawo gidan nan ban kula kowa ba sai kai, kuma ka san dai mun haɗu babu adadi". Halima ta fashe da kuka, ta zauna a kujera tana jin kamar daga yau ba za ta iya ƙara kwana a gidan Haruna ba. Ba ta jiyo muryarsa don haka ba ta san me ya tsara musu ba, ta dai ji shiru, sai kuma ta ga ya shigo ɗakin da sauri, ya canza kaya ya zo zai fita, ta tashi da sauri ta riƙe shi a fusace ta ce"Haruna da gaske Zainab ce ta zo da batun ka yi mata ciki? Akwai cikinka a jikin wata macen bayan ni?" Ya fizge da ƙarfi, a fusace ya ce"Dalla malama cika ni, kin san halin da nake ciki kuwa da har za ki riƙe ni?" Yana ficewa ta bi bayansa tana cewa"Uban waye ya saka ka a halin da kake ciki? Ka zo ka ba ni takardata na tafi, daga yau na bar aurenka har abada Haruna!". Maman Usman da komai yake faruwa a kunnenta, ta fito ta janyo Halima, tana fizgewa, kamar za ta kamo Haruna ta rufe shi da duka, ta shigar da ita ɗakinta, ta zaunar, Halima ta fashe da kuka tana cewa"Kar ki ba ni haƙuri, kar ki sake, ba zan ƙara kwana a gidan nan ba!". Maman Usman ta ce"Ba zan ba ki haƙuri yanzu ba, ki faɗi duk abin da kike ji zai sa zuciyarki ta yi sanyi, saboda na taɓa shiga irin wannan halin da kike ciki, amma kar ki manta da ƙaddara, kuma mu'mini shi ke yarda da ƙaddara ta alkahiri da ta sharri". Halima ra kifa kanta a kujera tana kuka. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN HARUNA Haruna ya koma wurinsu jiki na rawa, ya ce su je can gidan iyayensa a yi maganar, sai bin Zainab yake da mugun kallo, wacce ya gane kukan munafurci kawai take yi, don babu ɗugon hawaye a idonta, haka suka tarkata suka tafi gidansu, babansa ya tsufa sosai kuma yana fama da hawanjini, saboda haka yayan Haruna da mahaifiyarsa suka ce ba za su yarda ya ji ba, a zo a ɗaga masa hankali, Haruna ya ce da yayansa"Umar idan ban yi sirrina a nan ba a ina zan yi? Kuma kun san dole manyana su shiga maganar, don Allah ku taimaka min a warware matsalar, suna maganar ba za a cire ciki ba, kuma idan ta haihu sai na aureta, wallahi ba zan iya auren wannan makirar ba". Yayansa ya ce"Wannan matsalarka ce, ka fice daga gidan nan kawai ka san inda za ka kai su, sanda ka je ka aikata ai ba ka tuna makirar ba ce". Ya faɗa yana sake tare ƙofar gidan, dama ita mahaifiyarsa tuni ta shige ɗaki, tana kokowa da baƙinciki, tuno halin da matarsa za ta shiga idan ta ji zancen nan kawai take, ba ta taɓa tunanin ɗanta yana neman mata ba sai yau. Haruna ya fice ya koma inda suke a ƙofar gida, a sanyaye ya ce da su"Don Allah ku yi haƙuri, sun ce ba za su samu damar tattauna da ku a gidan nan ba, saboda babana yana kwance ba shi da lafiya, jin maganar nan zai iya ƙarawa rashin lafiyar ƙaimi". Yayar mahaifin Zainab ta yi masa mugun kallo ta ce"Wannan ba hujja ba ce, ai mu ma uwarmu tana can a kwance tun da ta ji labarin baƙincikin nan, saboda haka dole mu yi magana da wani naka!". Haka ya koma gidan ya sake lallaɓa yayan nashi da roƙo, har ya amince, ya fito ƙofar gida suna tattaunawa, Zaiban dai ta ce tun da suka dawo gidan nan ba ta yi wani saurayi ba sai shi, kuma Baaba ma ta tabbatar sanadin kama su ne ya sa ta tashi daga gidan, sannan aka karɓe layin wayar Zainab ɗin, to yanzu kuma kwatsam sai ga shi ta fara laulaye-laulaye, ana kai ta asibiti aka tabbatar da ciki, saboda haka ciki na Haruna, shi ma kuma bai musa ba, don haka ƙarshe a ka tsaya a kan zai aure ta bayan ta haihu. Haruna da wannan hukuncin bai yi masa daɗi ba, kamar zai yi kuka ya ce"Don Allah ku yi haƙuri ku cire zancen haihuwar nan, wannan ɓata suna ne, ku dubi makomar abin da za ta haifa, haka zai taso ana goranta masa, sannan ko gadona ba zai ci ba, don Allah a cire cikin nan". Ƙanin mahaifiyar Zainab ya ce"Wannan cikin fa sai ya zo duniya, babu dalilin da zai sa a cire shi, wannan hasashen naka da ka dogara da shi ba komai ba ne, ai ba kansa farau ba". Haruna ya ce"To matata fa? Kun san ina da mata Halima, kuma kun ce zan auri Zainab ta ya hakan zai faru?" Mutumin ya ce"Me zai hana shi faruwa? Ba da matar taka ka tsallake ka kai kan Zainab ɗin ba? Ka ga idan fa sulhu a gida bai yi ba, mu daga nan hizba za mu wuce". Ya girgiza kai da sauri ya ce"A'a sulhu ya yi, shi kenan idan ta haihu ɗin zan aureta". Suka gama tattaunawar aka tsaya a kan duk wata zai dinga kai mata dubu goma, yace ya amince. HALIMA Duk kalaman kwantar da hankalin da maman Usman take yi mata, ba ra fahimtar komai, har labari ta bata ita a yanzu haka mijinta yana da ɗa da wata, wanda aka yi cikinsa a waje, kuma har yau ba daina neman matan ya yi ba, tana haƙuri ne kawai, Halima ta ce"Ke za ki iya! Ni kuwa ba zan iya ba, ƙila zuciyarmu ba iri ɗaya ba ce, babu mamaki mijinki yana kyautata miki, ba shi da wani naƙasu sai ta wannan ɓangaren, shi yasa kika yi masa uzuri, ni kuma kina kallon kalar rayuwar da muke yi, abinci ma sai ya ga dama yake ba ni, sam ba ya sakin jiki ya yi fira da ni, kamar ba auren soyayya muka yi ba, idan na ci gaba da zama a gidan nan komai zai iya faruwa, maman Usman wani auren ba shi da amfani, wani auren wuta zai kai mutum!". Maman Usman ta ce"Idan kin bar nan kin je kin yi wani auren kina da tabbacin ba za ki tarar da matsala ba?" Halima ta ce"Allah zai dube ni, ya yi min canjin alkhairi". Daga haka ta shige ɗakinta, ta haɗa kaya mai yawa, ta fito, maman Usman ta ce"Yanzu Halima tafiya za ki yi, ba za ki jira ya dawo ki ji ta bakinsa ba?" Halima ta ce"Ai ba shi da sauran abin da zai faɗa mini kuma, zama ya ƙare har abada!". Ta ce"Tsaya na raka ki!" A tare suka tafi gidan, Mama tana kwance sai ga su Halima da uwar akwati, zuciyarta babu daɗi ta ce"Haba Halima, wai sai yaushe za ki yi haƙuri? Sai ka ce ciki kanki farau?" Halima ta fashe da kuka, suka zauna maman Usman ce duk ta zayyana mata abin da ya faru, Halima ta yi mata ƙarin bayani a kan kama su da ta yi da Zainab dumu-dumu, sosai hankalin Umma ya tashi, ranta ya ɓaci, ta ce"Yanzu dama irin rayuwar da kike yi kenan? Dama haka Haruna yake? Sai ya zo nan yana sunkuyar da kai kamar na Allah! Shi kenan ki zauna bari ya zo mu ji". Daga haka suka ci gaba da tattaunawa, maman Usman tana ta ba su haƙuri, ita har zuciyarta ba ta so auren ya mutu, sai da yaranta suka kusa tasowa daga makaranta ta yi musu sallama ta tafi, suna yi mata godiya, haka ta wuni a ɗaki tana jin ƙunci mara misali, sannan ta ƙudure ba za ta taɓa komawa gidan Haruna ba har abada. SADIQ Babu abin da yake sai hamdala, rayuwar gidansa tana tafiya a yadda yake so, sosai suke shan soyayyarsu da Kursum, da Hajiya ta ce sai ta yi wata ɗaya za a mayar da yaran, amma Kursum ta ƙi yarda, kwananta uku ta sa ya kwaso yaran, tana ba su kulawa cikakkiya, kullum cikin ƙara jansu a jiki take don har zuciyarta take son yaran, su ma sai suka saki jikinsu sosai, sam ba sa damuwa da rashin Yusra, sai dai wani lokacin sukan tambayi Kursum ɗin ina Momy ta tafi? Sai ta ce musu tafiya ta yi, amma ta kusa dawowa, a yanzu Sadiq yana tafiya wurin aiki ya dawo a sanda yake so, ya tarar da lafiyayyen girki kuma gida a gyare, kullum matarsa tana gida, ƴaƴansa suna gida babu yawon maƙota, ga yadda take bada kulawa sosai a kan karatunsu, idan lokacin wasa ne kuma ta biye musu a yi, ko kallo suke yi tana kusa da su tana ƙara yi musu bayani, abun yana burge shi sosai, don Yusra ba ta da wannan lokacin. Sati ɗaya da auren Yusra ta shiga damuwa sosai na abin da Sumayya ta yi mata, don ji ta yi ma duniyar gabaɗaya ta isheta, har wani ɓangare na zuciyarta yana bata kawai ta ajiye aikinta, amma sam ba ta ɗauki wannan shawarar ba, don babu amfanin baɗi ba rai, ta rabu da mijinta saboda aiki, sai yanzu ne za ta ajiye ta yi ihu bayan hari? Hakan zai sa Sumayya da maƙiyanta su ga cewar sun yi galaba a kanta, saboda haka ta daure tana ƙoƙarin mantar da kanta komai, ta ci gaba da zuwa aikinta, a yanzu ta daina damuwa da kula kowa, duk wanda ya yi ƙoƙarin janta a jiki gani take munafuki ne, saboda haka aikin gabanta kaɗai take yi, idan ba ta wurin aiki tana chames ɗinta, damuwarta ɗaya tunanin halin da yaranta suke ciki, don a yanzu tana zargin har soyayyar da Kursum take nuna musu duka ta bogi ce, ba ta taɓa zaton rashin yaran a kusa da ita zai dame ta ba sai yanzu. Watarana da daddare wajen ƙarfe tara, kewa da tunanin yaran suka dame ta, musamman jiya da ta yi mafarkinsu ta gansu tare da Kursum da Sadiq suna ta nishaɗi, ita kuma tana gefe tana kallonsu, ta ɗauki wayarta tana jujjuyata, kafin ta yi ƙundun-bala ta kira lambar Sadiq, ya ɗauka yana mamakin kiran nata, tun ranar da suka rabu ba su sake yin waya ba, ya yi mata sallama ta amsa ta ce"Sadiq ya kuke, ya gida". Ya ce"Alhamdulillah, gidana kowa yana cikin ƙoshin lafiya". Ta ce"Ma sha Allah! Ni ma ina cikin aminci". Ya ce"Alhamdulillah! Haka ake so". "Zan ajiye wayar!" Ya faɗa jin ta yi shiru. Ta ce"Dama ina son magana da yarana ne". Ya ce"Kin ga kuwa ina shago, yanzu nake shirin tashi dai, kuma na san zuwa yanzun sun yi bacci, sai dai next time ki tari lokacin da nake gida ki sake kira". "Ok" Kawai ta ce, ta katse kiran, hawayen da ta rasa ko na mene ne suka zubo mata, kuma ba ta damu da share su ba. GIDAN ALI Washegari da safe Ali ya shirya ya tafi wurin aikinsa, lokacin da zai ajiye aikin zuwa ya yi ƙafa da ƙafa ya faɗa musu ya ajiye aikin, saboda ya samu wani, don haka yau ɗin cike da jin nauyi ya koma, bayan sun gaisa ya faɗawa Ogan nasu ya dawo aiki, ya fasa wanda ya fara ɗin, Oga ya ce"Ayya! Ai kuwa Ali an samu matsala, ka san aikin rububibsa ake yi, dama akwai mutane da dama ma su yi mini maganar suna so, to kuma babu gurbi, shi yasa yanzun kana ajiyewa na samu wani ya maye gurbinka". Ali ya ji kamar an sare masa ƙafafunsa, don yana jin daɗin aikinsa sosai, da ƙyar ya samu aka yi masa hanya aka ɗauke shi, kafin shi dako yake yi a kasuwa, ya juya ya tafi jiki a sanyaye, sai ya rasa yadda zai yi, dama bai faɗawa babarsa ya ajiye aikin ba, sai ya zaɓi ce mata rage ma'aikata kawai aka yi, ta nuna rashin jin daɗinta, ya ce"Babu komai zan samu wani wurin in sha Allah!". Ta ce"To ni Ali ko Enugu za ka koma? Na ga wancen zuwan ka samu alkhairi". Ya yi ƴar dariya ya ce"Hajiya kenan, aikin Enugu akwai wuya fa,kuma ma ba a yi cikin Ramadan, za dai a bincika wani in sha Allah!" Ya yi mata sallama ya fita. A ƙofar gidan ya zauna ya kira Hajiya a waya, suka gaisa tana cewa"Ali ka watsar da ni". Ya ce"Wallahi Hajiya ba haka ba ne, yanayin aiki ne kawai da babu zama". Ta ce"Ni ma ka san Alhajina ya dawo gari fa, dayake a gida yake Ramadan, yanzu har sai bayan sallah zai koma, shi yasa ma ban kira ka mun yi sallama ba". Ya ce"A Hajiya sallama kuma?" Ta ce"E mana, Ramadan ai watan tuba ne da neman gafara, saboda haka idan ya zo nake kama kaina, na yi ta istigfari, kai ma ina fatan za ka tuba ka roƙi Allah Ya yafe maka zunubanka, bayan Ramadan kuma sai a ci gaba ko? Ai duk dole ce ta kawo hakan, Allah dai ya yaye mana kawai". Ali ya yi murmushi ya amsa da amin, suka ajiye waya, ya tashi ya ƙara gaba, haka ya yi ta yawon majalisa har la'asar ta yi, ya yi cefane ya koma gida, ya kai wa Maryam, ya jona wayarsa a caji ya ce mata zai je ya samo ƙanƙara, yana fitowa kawai ya ga wasu ƴan sanda guda biyu sun zo sun riƙe shi, da mamaki ya kalle su ya ce"Mene ne haka? Me na yi muku?" "Idan mun je office za ka ji komai!" Ɗaya ya faɗa yana ƙoƙarin saka masa ankwa. Ali ya ce"To ku tsaya na shiga na faɗawa matata". Ba su saurare shi ba, suka tankaɗa ƙeyarsa, cikin mota, wacce ta gida ce ma ba ta aikinsu ba, suka ja suka tafi, yana jin kamar ya yi tsuntsuwa ya faɗawa Maryam. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 GIDAN ALI Har aka sha ruwa babu Ali babu ƙanƙara, ga wayarsa tana ajiye sai kira ake yi, wanda ba ta damu da ɗagawa ba, sai da tara na dare ta yi sannan ta fara jin haushi, ta gama tsara yadda za ta kafa masa dokar kar ya sake shan ruwa a waje, ta yi ta zaune a falo tana jiransa, ganin sha ɗaya har ta yi, ta ɗauki wayarsa wai ko za ta kira wani abokin nasa idan suna tare, sai dai ba ta san mene ne password ɗinsa ba, don haka ta haƙura, ta je ta kwanta tana ta fargaba, ba yau ta saba kwana ita kaɗai ba amma yau ɗin ta ji tana tsoron gidan, haka dai ta yi addu'a tana ta juyi ta kasa baccin, sai dab da asuba ta samu baccin, alarm yana tashinta ta miƙe a firgice, sai da ta yi sallar asuba ta samu bacci cikakke, duk a tunaninta da safen zai dawo ya faɗa mata uzurinsa ko da na ƙarya ne, amma ta ji shiru azhar ta yi. Shi kuwa Ali bin su da kallo kawai yake, har aka ƙarasa staion, haka aka saka shi a seal babu bayanin komai, washegari ma sai azhar sannan aka fito da shi ana yi masa bayanin, an kama shi da sata ne a shagon Alhaji Sani, ana kyautata zaton shi ne ya ɗauki kuɗin da suka kai kimanin miliyan biyu, duk bayanin da Ali ya so yi ba su ba shi dama ba, suka ce ko ya faɗi inda kuɗin suke ko a kai shi kotu, ya kafe a kan shi bai ɗauki ko sisi ba, haka suka dinga dukansa ga azumi a bakinsa, amma amsar shi ɗaya ce bai ɗauka ba. Dab da magriba Maryam tana ta hada-hadar abincin buɗa baki, duk da ba lallai ta iya ci ba saboda damuwar da take kanta, yau ɗin a kwance ta wuni baya da mutum ɗaya da ta zo kitso ta yi mata, shi ma don ta ga baƙuwa ce ba ta taɓa zuwa ba, idan ta bata uzuri ba lallai ta fahimce ta, shi yasa ta daure ta yi mata, ko maƙota masu shigowa ɗaya-ɗaya ce musu take ba ta da lafiya. Banko ƙofar gidan da aka yi da ƙarfi ne ya sa ta ɗagowa a fusace, a tunaninta yara ne ta fara yi musu faɗa, sai dai ganin Ali ne ya shigo hannunsa da ankwa ta saki kwanon albasar da ta gama yankawa, sosai hankalinta ya tashi ganin yadda duka ya sassaɓa masa kamanni, ta bi ƴan sandan bayansa da kallo kafin ta ce"Mene ne yake faruwa? Me mijina ya yi muku?" Ɗaya daga cikinsu ya ce da sauran biyun"Ku shiga ku bincika ko'ina!". Suka tisa ƙeyar Ali har cikin ɗakin gado, yana kallo suka buɗe sif suka dinga watso kayan tsakar gida, sannan suka ɗage kafita suka bincike ƙasan gado, suka yi wa ɗakin kaca-kaca ba su ga komai ba, sannan suka fito suka yi falo, Ali yana kallon kayan sakawarsu dake watse a tsakar gida, idonsa ya sauka a kan condom, wanda kusan lokaci ɗaya suka gan shi da Maryam, ba ta lura da ya gani ba, saboda haka ta yi saurin cusa shi a cikin kaya, gabansa ya faɗi yana jin kamar har gara wannan masifar wannan sharrin satar da ta wannan bala'in da idonsa ya gane masa, "Maryam me ya haɗa ki da wannan abun!?" Gabanta ya shiga faɗuwa, hawayen da suke zuba tun da aka shigo da shi, suka ƙara gudu, ta ce"Wannan dogon bayani ne". Ya yi mata mugun kallo ya ce"Maryam bin maza kika fara da aurena? Wannan shi ne dalilinki na guje mini a shimfiɗa?" Ta girgiza kai da sauri, tana shirin yin magana suka ji ɗaya daga cikin ƴan sandan ya ce"Oga ga kuɗin a nan!". Duka gabansu ya faɗi, suka kalli ɗan sandan da ya janyo kwandon sharan gidan, wanda ba wata shara ce a ciki mai yawa ba, sai ƴan ledoji, ya ɗakko wata leda yana zazzage ta sai ga bandir ɗin kudi sun zubo daga ciki, Maryam ta ɗora hannu a kai tana yi wa Ali wani kallo mai ɗauke da tarin tambayoyi, shi ma Alin sosai mamaki ya kashe shi, amma ganin wannan masifar ta wajen Maryam ya rage masa wannan shock ɗin. "Wallahi ban san komai a kan kuɗin nan ba, sai dai idan kawowa aka yi, aka ajiye mini". Ali yana rufe baki ɗan sandan ya kai masa naushi yana cewa"Rufe mana baki, ɓarawon banza, dole ka girbi abin da ka shuka!". Ali ya ce"Ni ba ɓarawo ba ne, kuma duk me bi na da sharri a kansa zai ƙare". Ɗan sandar ya wanka masa mari, Maryam da take ji kamar ita ake duka a fusace ta ce"Kar ka sake dukan shi! Mijina ba ɓarawo ba ne, kuma duk wanda ya yi masa sharri Allah Ya yi mana sakayya!". Ko kallonta ba su yi ba, suka tisa ƙeyarsa suka fice yana yi mata mugun kallo, da sauri ta ɗauki mukulli ta rufe gidan, ta bi bayansu, sauri take kamar za ta tashi sama amma kafin ta bar cikin layin sun ɓacewa ganinta, a bakin titi ta tsaya duk mai babur ɗin da ta tare ta faɗa masa bayan motar ƴan sanda zai bi mata, sai ya yi mata kallon shashasha ya yi gaba, har aka sha ruwa tana titi, sai a lokacin ta tuna ma ashe girki take yi, ta koma gidan da sauri, ta sauke tukunyar shinkafar har ta kama tana ƙauri, ta sha ruwa, ta yi sallah, ta daɗe a sallaya tana kuka, don da ta ɗaga hannu don ta yi wa Ali addu'a sai ta rasa abin da za ta ce, kawai sai kuka, kafin daga bisani ta tashi ta shiga mayar da kayan sakawarsu dake watse a tsakar gida, kan gado kawai take watsa su, bayan ta ɗauke condom ɗin ta saka a jakarta, ta rufe ɗakunan, ta juye abincin a kula ta ɗauka ta fice daga gidan ta kulle. Kai tsaye gidan su Ali ta nufa, tana shiga ta fara kuka, hankali tashe babar Ali ta taso ta tare ta tana cewa"Maryam lafiya!? Mene ne ya faru, wani abun ya yi miki?" Maryam ta zauna tana ƙara sautin kukanta ta ce"Umma an kama Ali, yana can a kulle, sharrin sata suke so su yi masa, sun yi masa duka tun jiya yana can, ɗazu suka zo da shi aka yi bincike a gidan, suka fito da leda kuɗi a ciki bandir bandir..." Salatin Umma ne ya katse ta, ta dafe ƙirji tana cewa"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Yanzu Ali haka zai yi mana?" Maryam ta shiga girgiza kai ta ce"Wallahi Umma sharri aka yi masa, bai ɗauka ba, rabon shi da gida tun jiya da la'asar, kuma bayan ya fita ma na bawa yaro ya zubar min sharar, ledar taliya da ta pure water ne fa kawai a kwandon sharar, ni sam yau ban kula ma da wannnan ledar da suka fito da ita ba, wallahi sai dai idan da ita suka zo, macuta ne!" Ta fashe da kuka. Umma ta share hawayen da suka zubo mata ta ce"Shikenan! Allah Ya fitar da shi". Nan ta kira ƴan'uwansa a waya ta faɗa musu halin da ake ciki, ɗaya bayan ɗaya suka dinga zuwa, ga shi ba a san staion ɗin da yake ba, haka dai aka yi ta garari har aka gano inda yake, da ƙyar suka bari aka ganshi ma, suka ce gobe za a wuce kotu da shi, don haka ba za su saurari kowa ba, haka suka koma gida gwiwa a saluɓe, a kai ta jajanta abun, a nan Maryam ta kwana, ko abinci ba ta iya ci ba, da asuba ma sai da Umma ta matsa mata sannan ta sha shayi, ta ci abincin kaɗan. Gama sahur ɗinsu ke da wuya suka ji sallama a ƙofar gida, ƙanin Alin ne ya fita, babu jimawa ya dawo yana salati, Maryam da take a razane ta miƙe da tsaye tana tambayar me ya faru, ƙanin Ali ya ce"Wani maƙocinku ne ya zo, ya ce sun fito da asubar nan suka ga gidanku yana ta ci da wuta, ana ta kiran wayar Alin a kashe ke ma matarsa ta kira ki a kashe, yanzu dai ana can ana ƙoƙarin kashe wutar, amma ta ci sosai!". Jagwab Maryam ta zauna ta fashe da kukan tashin hankali, tana kallo Umma ta saka hijjabi ta fice, amma ita ta kasa ko motsawa, sai kuka take yi. Sai da gari ya yi haske sannan su Umma suka dawo, idanunsu da alamun sun yi kuka sosai, tare da babarta da yayyunta biyu suke, suka nufo inda take suna ba ta haƙuri"Ki yi haƙuri Maryam, Allah Ya mayar muku da alkhairi, amma komai ya ƙone". Yayarta ta ce"Ko kin bar wani abun na wuta a jone?". Ta ce"Globe kawai nake bari a kunne". Nan aka zauna ana ta jajanta abun. GIDAN HARUNA Sai da Halima ta yi biyu a gida sannan ya zo, duk wani bayani da ya so yi mata ta ƙi sauraron shi, ta ce takardarta kaɗai take jira, tun suna yi ƙasa-ƙasa har aka fara jin muryoyinsu, don shi ma faɗa ya fara yi sosai yana cewa ba zai sake ta ba, babarta da take cike da jin haushinsa ta ƙarasa inda suke a tsakar gida, ta ce"Haruna kai yanzu har kana da ƙwarin gwiwar ɗagawa Halima murya a cikin gidansu? Lallai namiji bai gaji kunya ba!" Ya ce"Umma cewa take fa na sake ta..." A fusace Umma ta ce"To meye idan ta ce? Da mene ne amfanin zama da kai? Ai idan ka ga Halima ta koma gidanka to ɗayan biyu ko dai ƙaddarar zaman ba ta ƙare ba, ko kuma ita ce ta haƙura ta yafe maka, amma aurenka kam ko ni na yi nadamarsa!". Zuciyarsa ta fara tafasa, ya ce"Amma kowa ya san dai wannan ƙaddara ce, ba ta wuce kan kowa ba". Halima ta ce"Babu wata ƙaddara, dama can haka kake, wallahi na yi nadamar aurenka Haruna, kuma ni da kai har abada!". Ya ce"Halima kar fa ki ga ina binki ki yi zaton ko wata uwar aurenki yake tsinana mini, wallahi haƙurin zama da kidahumar mace irinki kawai na yi, kuma ina duba cikin da take jikinki, don ta wani ɓangaren ma gara Zainab ɗin da ke, tun da haka ne ki je na sake ki saki ɗaya!" Daga haka ya tashi ya fice a fusace. Halima ta ce"Alhamdulillah!" Umma ta ce"Allah Ya sa hakan shi ya fi alkhairi, kar ki wani damu za ki samu wanda ya fi shi in sha Allah! Allah ba azzalumin bawansa ba ne, zai yi miki canjin alkhairi". Daga haka suka shiga ɗaki, Umma ta shiga yiwa Halima nasihar rayuwa, har ta ji jikinta ya yi sanyi. Washegari suka samu baƙuncin Anti Aisha, ƴar yayar mahaifin Halima ce, da take aure a wani garin, kwana biyu za ta yi, dama ta saba zuwa duk shekara siyayyar kayan sallah, ganin Halima a gida ta tambayi ba'asi, aka faɗa mata komai har da zancen cikin jikinta, nan ta ji kamar saboda samun maganin matsalarta auren Halima ya mutu, cikin mintuna ta gama tsarawa kanta komai, ta ce da Umma don Allah rana roƙon Halima ta koma gidanta da zama ko wata ɗaya ta yi ta huta, Umma ta ce indai Halima ta amince babu matsala, Halima ta amince, suka tsaya a kan za a kwaso kayanta na gidan Haruna kafin su tafi. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 ALI Ƙarfe bakwai na safe aka fito da Ali wanda yake a jigace, babu jimawa Daddy ya shigo yana kallonsa da makirin murmushi ya ce"Malam Aliyyu ya kake?" Ali ya ce"Alhamdulillah ala kulli haal!". Ya yi murmushi ya ce"Haba Aliyyu kalli fa yadda rayuwa ta canza maka a kwana biyu kacal, kuma duka kai ne ka ja wa kanka komai, Allah Ya sa dai zuwa yanzu wannan ya sa ka yi hankali". Ali ya ce"Indai tun farko kallon mahaukaci kake yi mini to har yanzu ma a haukan nake, kuma zan yi ta kasancewa a haka!". Daddy ya ce"Ban so mu yi haka da kai ba sam, me yasa ka satar mini kuɗi?" Ali ya ce"Da ni da kai mun san hakan ba ta faru ba, don haka ba ni da lokacin ɓatawa wurin amsa wannan tambayar". Ya ce"Ya ake ciki? Ko dai ka amince da tayin da na yi maka, ka fita daga wannan tarkon, sannan ka samu tagomashi mai tsoka ko kuma ka dawwama a haka". Ali ya yi murmushin takaici ya ce"Ba zan amince ba har abada, sannan ka daina tunanin kai ne ka saka ni a wannan halin, ballantana ka yaudare ni da cewar za ka fitar da ni, wannan yana zane cikin littafin ƙaddarata, saboda haka wani bawa ba zai iya canza komai ba!". Daddy ya jinjina kai ya ce"Da alama dai za ka sha wuyar rayuwa, saboda kana da taurin kai!". Ya miƙe tsaye ya ce"Ina yi maka jaje na gobarar da ta laƙume ruɓaɓɓen kejinka, ina kuma yi maka jajen sabuwar rayuwar da za ka shiga nan ba da jimawa ba". Ali ya ce"Allah Yana tare da ni, kuma shi zai bankaɗe isirin azzalumi irinka". Daga haka Daddy ya fice, aka mayar da Ali ɗakin da yake. Da yamma Maryam ta nemi rakiyar ƙaninsa, suka je wurin Ali, yana ganinta ya juya zai koma, ta je da sauri ta tsaya a gabansa ta ce"Don Allah ka yi haƙuri, wannan fushi da junan ba shi ne a gabanmu ba, ka fara fita daga wannan ƙangin, idan hankali ya kwanta sai mu zauna, na yi maka bayanin komai, na tabbata ka yarda da ni, don haka za ka fahimce ni". "Ke dakata dalla! Har kina da maganar da za ki faɗa mini na gamsu wacce ta fi abin da na gani da idona? Maryam don Allah kar ki sake zuwa inda nake, babu mamaki ma alkaba'ir ɗin da kike aikatawa a cikin gidan ne ya haddasa gobarar nan, kar ki sake zuwa inda nake na maimaita miki!". Ban da hawaye ba ta ce komai ba, ta gyaɗa masa kai alamar ta ji, ta juya ta tafi, ƙaninsa kuma ya ƙarasa suna magana. Ko jiransa ba ta yi ba, ta fice daga wurin, tana shiga adaidaita sahu ta fashe da kuka, wani irin yanayi take ji a zuciyarta, yau ita Ali yake zargi da aikata zina a cikin gidansa? Sam ba ta yi tunanin ɓoye masa wannan matsalar zai saka ta a matsala ba, da ta sani ta faɗa masa tun da farko, yanzu kuwa ba lallai ya fahimce ta ba, amma ita ma ai ta sha kama shi da hujjoji, sai ya musanta kuma ta nuna ta yarda har ta bar komai ya wuce, sarai ta san yana neman matan take zaune da shi a haka, ashe shi ko da ta tabbata tana yi ba zai iya yi mata uzuri ba, tunani take yi me yasa maza da yawa ba sa taɓa yi wa mace wannan haƙurin, idan suka samu mace da irin haka shikenan zama ya ƙare a tsakaninsu, iyayen miji da abokai ba sa taɓa yayyafawa abun ruwan sanyi a samu daidaito, sai dai su ce ya sake ta ba macen zama ba ce, amma idan mace ce ta kama miji da haka, kowa sai ya dinga ba ta haƙuri, a ce ta zauna saboda ƴaƴanta, kuma idan ta bar gidan ba ta san wanda za ta aura ba, haka za ta haƙura ta zauna ɗin har ma ta saki jiki su koma zaman lafiya, wannan adalci ne kuwa? Gidan iyayenta ta wuce, jikinta duk a mace, ana ta shigowa ana jajanta mata, ita kuwa kalaman Ali da irin kallon tsanar da yake jifanta da shi ne kawai yake yawo a zuciyarta, kafin dare zazzaɓi ya rufe ta ruf, a ranar kuma ƙaninsa ya zo ya ce Alin ya ce idan wayarsa tana hannunta ta bada, ta ɗakko ta ba shi ya tafi. Haka aka bar Ali a nan ba a je kotun ba, har tsawon sati biyu, gefe guda kuma ƙaninsa yana ta warkajaminsa a wayarsa, don Ali ya faɗa masa password ɗinsa, ya ce ya kira masa wani abokinsa wanda suka yi karatu tare, a zatonsa ko zai samu wani taimako ta ɓangarensa, sai ya ji lambar ma ba ta shiga, tun daga nan yake ta amfani da wayar, idan an kira ya ɗaga ya faɗawa mutum ga halin da Ali yake ciki. Ana haka ne watarana Hajiya ta kira Alin, don ta ji labarin gobarar da aka yi a gidansa tun a ranar, sai dai ta yi mamaki da bai faɗa mata ko jaje ta yi masa ba, don haka yau ɗin ta kira shi ta ji halin da yake ciki, ƙaninsa ya ɗaga ba tare da ya bincika ya ji ko wace ce ba ya yi mata bayanin komai, har staion ɗin da yake a rufe ya faɗa mata, sosai hankalinta ya tashi, kuma a ranar ta shirya ta tafi inda yake. Saranda Ali ya yi ganin baƙuwarsa ta yau, ya ɗan saki fuska ya ce"Hajiya". Fuskarta da damuwa sosai ta ce"Ali mene ne ya faru? Da gaske ka ɗaukar musu kuɗi?" Ali ya sauke numfashi ya ce"Wallahi Hajiya sata ba halina ba ce, tun da na fara zuwa wurin nan idan na taɓa satar musu nera biyar Allah Ya sa ta zama ajalina". Hajiya ta ce"Ni ma na yi mamaki, ba a dogon zama da ɓarawo bai nuna ba, na sha gwadaka Aliyyu, kai ba ɓarawo ba ne, waye wannan mutumin da yake son bin ka da sharri?" Ali bai ɓoye mata komai ba, duka ya faɗa mata wane ne Daddy da sanadin haɗuwarsu Farha, da buƙatar da ya zo masa da ita, wacce ko yau ya amince ya san zai fita daga wannan halin. Hajiya Zuwaira ta shiga jinjina kai, ta san Alhaji Sani a kasuwa, kuma ta san yana da ƙarfin iko tun da yana da kuɗi, ba za ta iya karawa da shi ba, musamman ma yanzu da take taka-tsan-tsan tun da mijinta yana gida, amma sam ba za ta iya barin Ali a wannan halin ba, don haka dole za ta san abun yi, suka yi sallama da Ali a kan za ta dawo gobe jo jibi, ta tafi ranta a dagule, kai tsaye unguwar su Farha ta nufa, kamar yadda Ali ya kwatanta mata, don sanin ta inda za ta fara gudanar da aikinta. GIDAN HARUNA Washegari an je kwashe kayan Halima aka tarar babu kujeru, don su Haruna ya siyar, ya bawa Zainab kuɗin ya lallaɓe ta, ta amincr za ta zubar da cikin jikinta tare da yi mata alƙawarin ba zai fasa aurenta ba, ko don ya cusawa Halima takaici, haka kuwa aka yi ta karɓe kuɗin ta zubar da cikin ba tare da ƴan gidan sun san da gangan ya zube ba. Ƴan'uwan Halima sun so tada rigima Anti Aisha ta ce a yi haƙuri za ta biya kuɗin, aka kwashe sauran kayan, washegari suka tattara suka tafi. Alhaji Bashir mijin Aisha mai rufin asirine, auren soyayya suka yi kuma zaman lafiya sosai, matsalarsu ɗaya ce rashin haihuwa, shekara takwas da aurensu Allah bai ba ta haihuwa ba, kuma an yi bincike matsalar daga wurinta take, an sha yi mata aiki ba a dace ba dai, sam babu kyakkyawar alaƙa tsakaninta da dangin shi, saboda halinta na rashin son mutane, da ƙasƙanci ta tsani a raɓi mijinta, tana baƙincikin ya ɗauki abu ya bawa wani nashi, to ita ma ba ta bawa nata ƴan'uwan, ita dai ta tara kawai ta yi bushasharta son ranta, ga ta da mugun son jiki, ita ba ɗa ba, ba kuma fita aiki take ba, amma ba ta iya rayuwa babu ƴar aiki, aikinta kawai ta ci kwalliya ta hakimce a falo tana ciye-ciyenta, ta yi kallo ta yi chatting, komai tana daga zaune take sawa a yi mata, ɗakin mai gidan ne kaɗai take gyarawa, kuma ba kullum ba, a son jikinta da zai yiwu ƴar aiki ta yi mata wanka to tabbas za ta saka ta, ga ta da faɗa laifi kaɗan za ta hau yarinya da masifa, zagin cin mutunci da gori kala-kala, ga maƙo ko ƴar kyauta ba ta yi musu, halinta ya sa ta yi canje-canjen ƴan aiki da dama. Ta sani ko ba yau ba dole mijinta zai ƙara aure, saboda yadda danginsa suke caccakarsa a kan hakan, shi kuma shakkarta ce ta sa shi kasa yin aure, mutum ne mai son zaman lafiya, sannan yana son Aisha sosai, shi yasa ba ya son abin da zai ɓata ranta, saboda mace ce mai zafin kishi, ko ƴan aiki sun sani, indai yana gida ba su isa su fito babu hijjabi ba, haka ko gaishe shi suka yi wani lokacin za ta bi su da kallon banza. A yanzu ba ta da burin da ya wuce mijinta ya auri Halima, saboda ta san ba ta da rawar kai irin na matan zamani, ko da ta haihu ba za ta ba ta matsala ba, sannan ta kere mata sosai a wayewa kuma ta girme mata, don haka ba ta jin za ta iya ƙwace mata miji, amfaninta a gidan zai zama ta haihu ne kawai, tana kyautata zaton Halima ba za ta yi wayewar da za ta daina girmamata ba. Kwanansu Halima uku a gidan, ta kasa sakin jikinta, duk da yadda Anti Aisha take nuna mata ta saki jiki ra huta, idan tana son zaman gidan ma ta yi zamanta, ta gama idda ta samu miji ta yi wani auren, yawanci Halima tana ɗaki, takan shiga kitchen ta taya ƴar aikin gidan aiki saboda ba ta saba zama haka babu aiki ba, har suna ɗan taɓa fira da yarinyar, tana mamakin yadda Antin ta sakarwa ƴar aiki gyaran gidan duka har da girki. Kwanan Halima huɗu a gidan, bayan an sha ruwa ta idar da sallar isha'i ta fara ciwon mara, nan da nan jini ya yanke mata, hankali tashe ta faɗawa Anti Aisha, sai ta ga ba ta wani damu ba, ta ce bari mai gidan ya dawo a kai ta asibiti, haka ta kwanta ta dinga murƙususu, har sai da cikin ya zube, Aisha da take leƙenta ta window ta shigo, tana yi mata sannu, sai a lokacin ta kira ƴar aikin gidan ta taimakawa Halima ta gyara jikinta, sannan suka tafi asibiti da Aisha, kwananta biyu aka sallame ta, don sai da aka yi mata wankin ciki, kuma an ƙara mata jini leda biyu. Bayan sun dawo gida Aisha ta kira waya ta faɗawa Umma abin da ya faru, ganin Umma ta shiga damuwa ta ce"Haba Umma wannan ba abun damuwa ba ne, dama mene ne amfanin haɗa zuri'a da namiji irin wannan? Kawai mu yi addu'ar Allah Ya sa hakan shi ne alkhairi, ba ga shi yanzu ta gama idarta ba? Sai a faɗawa mijin nata don ya tabbatar da ta gama idda ya rasa ta har abada". Da wannan ta kwantarwa da Umma hankali, musamman da suka gaisa da Halima ta faɗa mata yanzu lafiya ƙalau take. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 YUSRA Yau ta tashi da kewar ƴaƴanta, tun da ta bar gidan ba su taɓa yin waya ba, ballantana ta gansu, sau biyu tana kiran Sadiq saboda ya haɗata da su sai ya ce ba ya gida, yau ma kiransa ta yi, suka gaisa sama-sama, ta ce"Sadiq ina son magana da yarana, idan kuma ka sauke matsayina na uwa daga kansu sai ka yi mini bayani". Ya yi murmushi ya ce"Ai ba a canza uwa, Yusra yaranki har yanzu ba su da wacce ta fi ki matsayi, Allah Ya sa kar na manta idan na koma gidan na kira ki ku gaisa". Ta ce"Ok, ina jira". Har za ta katse kiran ya ce"Ko kuma ki kira Kursum, tun da suna gida". Ba ta ce komai na ta kashe wayar. Yana komawa ya kira ta, ya miƙawa yaran, suka shiga murna, suna tambayarta yaushe za ta dawo? Ta yi murmushin yaƙe ta ce"Afna ba zan dawo ba, ba ga Kursum tana yi muku komai ba?" Afna ta ce"E tana yi mana komai, kuma ma Daddy ya ce ya aureta yanzu, a nan za ta yi ta zama". Ta ce"Kun ji daɗin hakan ko?" Ta ce"E sosai, kullum tare muke wasa". Kursum ta karɓi wayar ta ce"Anti ina wuni, ya aiki?" Yusra ta ce"Na wuce ajinki Kursum, ko wacce kuka haɗa makircin tare babu yadda za ta yi da ni, domin ni kainuwa nake dashen Allah, kuma idan na yi niyyar dawowa gidana dole ki fita ki bar mini!". Sadiq ya karɓe wayar, yana yin hanyar fita daga ɗakin ya ce"Haba Yusra, wannan ba girmanki ba ne". Yusra ta ce"Ba ka san komai ba, ba ka san da wacce kake rayuwa ba, don haka ka yi taka-tsan-tsan, kuma ka kula mini da yarana, don wallahi idan ta cutar da su ba zan bar ta ba!". Sadiq ya ce"Yusra kenan, me yasa kika zaɓi rabuwa da ni, duk da kin san ba za ki iya cire ni a zuciyarki ba?" Ta ce"Tun ranar da na san za ka aure ta na cire ka a zuciyata, saboda haka kar ka yi zaton kishinka nake yi, aurenka da Kursum duka shiri ne, makircin Sumayya ne ita ce ta tsara komai, saboda ta tarwatsa zamana da kai, duka ta yi komai ne don ta yi ramuwar gayya, Sadiq Sumayya ba ta haƙura ba ashe, tana nan tana dakon baƙincikin rabuwa da ita da ka yi, ta ce babban burinta ta ga mun bar inuwa ɗaya, yanzu burinta ya cika, ta kuma aura maka shu'uma irinta, saboda haka ka yi hankali da ita". Daga haka ta kashe wayar, hawaye suka zubo mata, tana nadamar biyewa Sumayya, har ta yi mata yardar da za ta nemo mata ƴar aiki. Sadiq kuwa saranda ya yi riƙe da wayar, yana neman mizanin da zai auna maganganun Yusra, sosai ya yarda da son da Kursum take yi masa, shi yasa ya fi yarda da kishi ne ya sa Yusra faɗin hakan, koma dai shiri ne shi kam ba shi da damuwa, don ya samu Kursum a yadda yake so, tana kula da gidansa sosai, saboda haka ba zai ɗorawa kansa wani binciken banza ba ya bincikowa kansa damuwa, ya ɗage kafaɗa ya koma ɗakin. Ya zauna kusa da Kursum yana nazartarta, ganin jikinta ya yi sanyi, ya ce"Baby lafiya kuwa?" Ta yi murmushin yaƙe ta ce"Lafiya ƙalau, me ka gani?" Ya ce"Kar maganganun Yusra su dame ki, tana so na sosai, kuma kin ga ko babu so akwai shaƙuwa, mun yi shekaru tare da ita, dole za ta yi kishina, sannan ba zai yiwu na ce na daina waya da ita ba, tun da da ƴaƴanta a hannuna". Kursum ta ce"Babu komai fa, duka na san wannan, Allah Ya huci zuciyarta". Daga haka suka shiga firar su. ALI Kuɗi Hajiya ta saki ta haɗa da makircinta, wajen yin bincike, cikin kwana uku ta san komai na rayuwar gidan Daddy, baki da baki ta tattauna da ƴar aikin gidan, ta tabbatar mata ta daɗe tana zargin Alhajin suna keɓewa da Farha, ta tattara duk wasu hujjoji a hannunta, sannan ta samu lambar Salma ta faɗa mata komai. Sosai hankalin Salma ya tashi da ta ji zancen ƙanwarta na ɗauke da ciki kuma na mijinta ne, don duk da Hajiya ba ta tabbatar ba hakan ta faɗa mata, a kwana biyu da suka wuce ta lura da yanayin Farha kamar mai ciki, sai dai ba ta wani zurfafa bincike ba, don ba ta taɓa zaton hasashenta zai tabbata ba. Wani abu da ba ta sani ba shi ne, a satin farko na azumi sosai aka sha gumurzu a cikin gidan nata, tsakanin Farha da Daddy, don ta gano da cikin jikinta, kai tsaye ta samu Daddy da zancen ta ce masa nasa ne, kuma bai yi musu ba don ba shi ma da hujjar kare kansa, nan ya roƙe ta kan ta zubar, ta ce ba za ta zubar ba sai ya bata miliyan biyar, nan take ya fara yi mata kallon mahaukaciya, ya tabbatar mata ko naira biyar ba zai bata ba, kuma dole ta zubar da cikin, ita kuwa ta kafe akan dole sai ya bata, sosai abun ya dame shi, ya yi nadamar shiga huruminta tun farko, lallai zina babbar masifa ce, yarinyar da ta taso a ƙarƙashin kulawarsa ya riƙe ta kamar ƴarsa, cinta, shanta, sutura, magani da karatunta duka shi ne, yau ita ce take yi masa rashin kunya, har tana neman wasu manyan kuɗi daga wurinsa a matsayin sharaɗi? Shi yasa ya so Ali ya amince ta yadda ko ƙwai ya fashe zai kai ƙara kotu ya ce sharri ta yi masa, a daidai lokacin sai Ali ya bayyana ya ce tabbas cikin shi ne, dole Salma ta amince tun da ta san sun yi soyayya, to sai Alin ya cuce shi ya ƙi ba shi haɗin kai. Yana matse Ali ne kawai saboda ya amince, ba don shi ma yana cikin hayyacinsa ba, Allah ma Ya sani yana son matarsa, ba ya son abin da zai zama silar rabuwarsu, sannan idan wannan ƙwai ya fashe da wane idon zai kalli duniya? Ba kowa ne ya san shi da wannan fuskar ba, wannan ɓoyayyen sirrinsa ne. Tsam Salma ta tashi bayan ta gama duba duka saƙonnin da Hajiya ta turo mata, ta gwada kiran lambar layin ba ya tafiya, dama ta ayyana za a yi hakan. Kai tsaye ɗakin Salma ta shiga, zaune ta same ta, ta haɗa kai da gwiwa tana hawaye, ta ɗago da sauri tana daidaita nutsuwarta jin shigowar Salman. Ta ƙasara wani zargi na ɗarsuwa a zuciyarta, ta ce"Farha, kukan me kike yi?" Ta fara share hawayen, sannan ta ce"Babu komai Momy, kaina ke ciwo kaɗan". Salma ta ce"Ok, ki sako hijjabinki za mu fita". Farha ta tashi ta saka hijjabi, suka fita, Salma tana tuƙa motar tana ta karanto Allahumma la sahla a zuciyarta, har suka ƙarasa asibitin da suka saba zuwa, gaban Farha ya fara faɗuwa ta ce"Momy waye babu lafiya? Dubiya za mu je?" Salma ta ce"Ke ce ba ki da lafiya, ina so a duba mini ke na san me ya kawo miki ciwon kan nan". Ƙirjinta ya buga da ƙarfi ta ce"Momy, amma fa na sha magani, kuma ma..." Salma ta ɗaga mata hannu ta ce"Gani ya kori ji Farha". Daga haka suka shiga, Farha tana ji kamar ta zura a guje, cike da fargaba Salma ta yi wa nurse bayanin abin da ya kawo su, nan take aka yi wa Farha gwaje-gwaje, aka gano cikin jikinta na watanni uku, da ƙyar Salma ta iya riƙe kanta, ba ta kula Farha ba, har suka koma gida, ita kuwa kuka kawai take yi a hanya. Sai da ta shiga ɗakinta ta zauna, sannan Salma ta bi bayanta, ta nemi wuri ta zauna ta harɗe hannu ta ce"Farha cikin jikinki na wane ne?" "Ni ma ban sani ba" Ta ba ta amsa cikin kuka. Salma ta ɗauke ƙwallar da ta zubo mata, tana bawa kanta ƙwarin gwiwa ta ce"Ni bari na sanar miki, cikin jikinki na mijina ne, a zahiri ni yake aure, a baɗini kuwa ni da ke duka matansa ne, kun ci amanata sau shurin masaƙi, har ta kai kin samu cikinsa, a yanzu rawa iri ɗaya muke takawa a gidan nan da ni da ke, babu wani bambanci, ina riƙe ki a matsayin uwa, ina ta ƙoƙarin ganin shi kin ba shi matsayin uba, ashe duka a fanko kuke kallona, shashasha mara hankali da amfani, Farha kin cuce ni, kin cuci kanki, ina roƙon Allah Ya yi mini sakayyar abin da kuka yi mini, indai mijina ne na bar miki shi har abada, ki haihu ya aure ki, ƴaƴana naki ne, na ba ki, ki yi musu ruƙon da kika so, zan yi nisa da duniyarku ballantana ganina ya sare miki gwiwa, na gode Farha!". Daga haka ta tashi ta fice daga ɗakin, tana fita ta ga Alhaji tsaye yana yi musu laɓen da ya saba, sai dai wannan karon ko zabura bai yi ba ballantana ya gudu ko ya wayance, saboda maganganun Salma sun sare masa gwiwa, yanzu wasan da suke bugawa ya zo ƙarshe, yau ɗin rana wanka ce babu batun ɓoyon cibi, saboda haka dole ya fuskance ta, su baje ta a faifai su tsince tsakuwa daga cikin aya, tun da ta san komai, duk a tunaninsa Farha ce ta fito ta faɗi gaskiya, don haka yake ta jinjina daƙiƙancinta. "Salma!" Ya kira sunanta, a sanyaye. Tana ƙoƙarin danne damuwarta ta ce"Na'am". Ya ce"Duk wanda aka ce ya yi haƙuri an cuce shi ne, tun da kin san komai, ba ni da abin da zai ce miki sai dai ki yi haƙuri..." Ta ɗaga masa hannu ta ce"Idan kana so na fahimce ka, ka yi gaggawar fitar da Ali daga halin da ka saka shi, sannan ka ɗauki kuɗi ka biya shi asarar da ya yi, ta gobarar da ka haɗa a gidansa, kuma ka nemi yafiyarsa, sannan ka ba ni lambarsa don na tabbatar da ka aikata hakan, sai na saurare ka!". Ta juya za ta tafi, ya sha gabanta ya ce"To babu damuwa, zan yi duk yadda kika ce, don Allah ki yi haƙuri wallahi ƙaddara ce da hau". "Ok" Kawai ta ce, ta shige ɗakinta, zama ta yi tana jin wani irin yanayi, ji take kamar ta ɗora hannu a ka ta fara kurma ihu ko za ta ji sassauci a zuciyarta, tana ta zargin kanta da ciwon hauka, to idan ba haka ba me take yi da har haka take faruwa a gidanta, har mutanen duniya su fi ta sanin sirrin gidanta, ashe duk tsirara ake kallonta ba ta sani ba, ta yi nasarar fashewa da kuka, ta shiga yi babu ƙaƙƙautawa. Kai tsaye Alhaji wurin Ali ya tafi, ya ba da damar a sake shi, bayan an fito da shi, jiki a sanyaye ya kalli Alin ya ce"Idan ka koma gida, ka lissafa asarar da ka yi sanadin gobarar gidanka, ka faɗa mini, zan biyaka". "Ba na buƙatar biyar ɗinka, komai ina jingina shi ne da ƙaddara, kai ne ka saka mini wuta ko ba kai ba, wannan matsalarka ce, zalincin da ka yi mini na barka da Allah!" Ali ya faɗa yana yi masa mugun kallo. Daddy ya ce"Kar ka cuci kanka, don na san ba ka da tudun dafawa a yanzu, ina jiran kiranka!". Daga haka ya fice daga wurin, sannan ya ce da ƴan sandan su kai shi har gida, don a ga gidan da yake. Haka kuwa aka yi, har ƙofar gidansu aka sauke shi, yana shiga mahaifiyarsa ta tashi ta tare shi tana fashewa da kuka, wanka ya fara yi, ya kwanta yana jin alamun saukar zazzaɓi a jikinsa. Yana jin lokacin da Hajiyar take waya tana faɗawa Maryam ya dawo, sai bayan an sha ruwa da ƙaninsa ya dawo daga aiki ya ba shi wayarsa, kuma ya dinga yi masa lissafin mutanen da suka yi waya, nan ya shiga dudduba wayar, ya ga an yi waya da Hajiya sosai, sai da babarsu ta matsa daga wurin sannan ya tambaye shi me suka tattauna da Hajiyar? Ya yi masa bayanin komai, ya sauke ajiyar zuciya da ya gane cewar ƙanin nasa bai gano alaƙarsu ba. Suna cikin tattaunawa sai ga mutane sun yi sallama suna shigo musu da kayan abinci, Ali ya miƙe tsaye ransa a ɓace ya ce"Wannan kayan fa daga ina!?" Gabansa ya faɗi jin sun cr wata Hajiya ce ta aiko su, kuma ga ta nan shigowa, tuni gumi ya fara karyo masa, yana tunanin me yasa za ta yi masa haka? Ya yi saurin ficewa don ya tare ta su gama komai a waje, yana fita ya ga Maryam tana tahowa ɗauke da kular abinci, kallo ɗaya ya yi mata ya mai da hankali kan matar da take fitowa wacce yake gani kamar ya santa. Ta ƙaraso inda yake ta ce"Sannu Aliyyu, an fito lafiya?" Ya ce"Lafiya ƙalau Hajiya, amma me ya kawo ki gidanmu?" Maryam da kishi ya gama turnuƙo ta, a fusace ta ce"Da gaske tambaya kake yi? Zuwa ta yi ku ɗora daga inda kuka tsaya, tun da ta yi kewarka!". Ta kalli matar ta ce"Dama ke ce Hajiyar da kike son jefa mijina ga halaka? Ke kuwa Mama me kika rasa a gidan duniya da kika zaɓi aikata zina da yara sa'annin ƙannanki?" A fusace Ali ya ce"Idan ba ki bar ƙofar gidan nan ba sai na wanka miki mari wallahi! Ba ki da hankali ashe? Ba ki san mace ba kawai ki hau faɗa mata maganganu haka?" Salma ta ƙaraso za ta dafa Maryam, ta goce tana yi mata kallon tsana, Salma ta ce"Mu shiga daga ciki don Allah, ƙila idan na yi muku bayani ki fahimce ni, ko da ba ki janye munanan kalamanki daga kaina ba". Daga haka ta yi cikin gidan, Maryam ta bi bayansa, don haka shi ma ya ga ba shi da zaɓin da ya wuce ya shiga, sai dai cike yake da fargabar abin da ta zo da shi. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Tsaf Salma ta ba su labarin duk abin da yake tsakanin Ali da mijinta kamar yadda Hajiya ta turo mata, da ta gama ta ɗora da faɗin"Idan za ku yi shari'a da shi babu wanda zai ga laifinku, to sai dai a sha'anin ƙasar nan zai yi wuya ku yi nasara, tun da yanzu indai mutum ya fi ka ƙumbar susa ya fi ƙarfin shari'a da kai". Ali ya ce"Dama ni ba ni da niyyar shari'a da shi, komai da ya faru ƙaddara ce, kuma zai wuce in sha Allah!". Ta ce"Ya ce ka faɗi asarar da ka yi ya biya ka, ka lissafa?" Ali ya girgiza kai ya ce"Babu komai, Allah shi zai mayar mini da wannan". Salma ta ce"A'a Aliyyu tun da har ta tabbata shi ya aika aka saka maka wuta bai kamata ka ƙi karɓa ba..." "Na rantse ba na so, ba zan karɓi ko sisin shi ba, wannan abincin ma ku koma da shi, akwai ranar hisabi" Ali ya katse ta da faɗin hakan. Salma ta ce"Ba zan matsa maka ba, abinci ni ce na siya maka da kuɗina, kana da mata da iyaye, a yanzu haka ba ka da wani aikin yi, ga azumi ana yi, kar ka ce ba ka buƙata, ko ba a yi haka ba, zan iya taimaka maka saboda neman lada". Ya yi shiru, jin babarsa ta fara yi mata godiya, ta ɗakko kuɗi a jakarta dubu ɗari biyu ta ajiye masa, ta tashi ta fice, Maryam ta bi bayanta jiki a sanyaye, sai da suka fita ƙofar gida ta ce"Ki yi haƙuri baiwar Allah, na yanke miki hukunci cikin jahilci". Salma ta ce"Babu komai Maryam, ina ga halin mazajenmu ya zo ɗaya, shi yasa, ki ƙara haƙuri da jansa a jiki ƙila zai gyaru nan gaba". Daga haka ta shige mota ta tafi. Maryam ta ja ƙafa ta koma ciki, yana zaune a inda ta bar shi suna tattaunawa da Hajiya, ta ce"Maryam ku shiga ciki mana!". Ta amsa da to, sannan ta shiga ɗakin, ya bi bayanta don kar Hajiyan ta zargi wani abu. Ta ɗauki faranti ta zuba masa abincin da ta kawo masa, ta miƙa masa, bai kalli abincin ba ya ce"Maryam ya muka yi da ke? Ba na faɗa miki kar ki sake zuwa inda nake ba?" Ta ce"Matsaloli da dama zama kawai suke buƙata a tattauna su a fahimce su, rashin hakan ne yake neman lalata zamanmu, abin da ya faru yanzun nan na bayanin matar nan ya isheka ƙarin bayani". Jin bai ce komai ba, ta shiga ba shi labarin duk abubuwan da suka faru, har zuciyarsa ya yarda da ita, ya nemi ta nuna masa saƙon ta ce gogewa take yi, ya nisa ya ce"Ki yi haƙuri da zargin da na yi miki". Ta ce"Dama ban yi fushi ba, amma a bayanin fitowarka na fahimci akwai wacce ta shirya komai...". Ya ce"Kin ga don Allah kar ki wani zurfafa bincike!". Ya karɓi wayarta ya ce bayan kwana biyu zai dawo mata da ita, sannan ya rakata har gida, ya shiga suka gaisa da iyayenta, ya yi musu godiya. Duk bincikensa bai ga komai a wayarta ba, don an lafa da turo mata saƙonnin, ya dai bar wayar a kunne, da asuba yana ganin shigowar saƙo ya duba ya ga baƙuwar lamba ce take faɗa mata mijinta ya dawo, ta bincika za ta ji karuwarsa ce ta fito da shi, za su ɗora daga inda suka tsaya, saboda haka ta bar wahalar da kanta, ita ma ta amince su haɗu ya ɗebe mata kewa da baƙin cikin mijinta, Ali har yana karkarwa ya mayar da amsa a matsayin Maryam ya ce ni ma zuwa yanzu na gaji, saboda haka a shirye nake mu haɗu da kai ko a yau ma, bai daɗe da turawa ba aka dawo da amsar gobe zai faɗi wurin da za su haɗu. Da sassafe yana tashi daga baccin da ya koma ya duba wayar Maryam ya ga an turo inda za a haɗu, da lokaci ya bada amsa da zai zo in sha Allah. Yana ɗaukar tashi wayar ya ga saƙo da baƙuwar lamba, ana faɗa masa ya saka ido sosai a kan matarsa, yawon banza take yi lungu-lungu, yanzu haka yau idan ya je wuri kaza da ƙarfe kaza tabbas zai ganta ta je wurin wanda suka saba haɗuwa. Ya riƙe baki yana tunanin wane ne wannan yake ƙoƙarin raba shi da matarsa? Nan ma amsa ya mayar da ya gode kuma zai je. Ya kira Maryam ya ce ta shirya zai zo su fita, ƙarfe goma ya je gidansu, duk ya yi mata bayani ya nuna mata saƙon, ya ce ta je, za ta fara yin gaba sannan ya bi bayanta, a tsorace ta kalle shi ta ce"A kan me? Idan wani abu ya faru kafin ya zo ɗin fa?" Ali ya ce"Babu abin da zai faru, ba fa hotel ba ne, wurin shan iska ne kawai, kuma kina tafiya ina bin bayanki". Ta bi shi suka tafi, tana sauka daga adaidaita sahu ta ji shigowar saƙo, ta duba ta ga haƙuri yake ba ta na lattin da ya yi, amma ta zauna yana nan zuwa, ta nemi wuri ta zauna tana rarraba idon ta inda zai fito, Ali da ke can nesa da inda take a zaune, shi ma sai ga saƙo ta wayarsa, ana faɗa masa yanzu haka matarsa tana wurin ya hanzarta. Babu jimawa ya ga wanda ke zaune a kujerar kusa da shi ya fara waya yana cewa"Hajiya aikinki fa saura ƙiris ya cika, komai yana tafiya daidai, yanzu haka dai ga matar Ali zaune daram a kujera tana jirana, shi nake jira ya shigo sai na ƙarasa wurinta, ba zan nuna mata da ni take connecting ba, kawai zan je mata ne kamar yanzu na ganta na ƙyasa, ya ganmu a tare dai kawai ya wadatar". Ya kwashe da dariya yana cewa"Ba ki da matsala Hajiya, bari ya ƙaraso". Ali da ya kasa danne zuciyarsa ya taso a zuciye yana ƙarewa tsililin saurayin kallo, kafin ya ce"Ai na ƙaraso, me kuma kake jira? Kai wane irin daƙiƙi ne ta ba ka aiki babu hotona? To ni ne Ali, Hajiya Aisha ce ta turo ka ko?" Maryam ta taso da sauri ya ƙarasa. Saurayin ya juya zai tafi, Ali ya damƙo shi, ya fesa masa mari, ya ci kwalarsa ya ce"Wace ce ta turo ka? Hajiya Aisha ko Zuwaira?" Ya raba sunan biyu, don ya kasa tantance sunanta na ainihi. Matashin ya fara fizgewa, nan dambe ya kaure a tsakaninsu, da ƙyar aka raba su, matashin yana zagin shi da cewar mazinaci mai bin matar aure, Ali yana kumfar bakin sai ya kulle shi, Maryam kuwa tun da ta ji kalmar mazinaci mai bin matar aure ta sarewa lamarin mijinta, don ba ta taɓa zaton Hajiyar tana da aure ba, ta ƙaraso ta kalli Ali a cikin jama'a ta ce"Don Allah ya isa haka, ban ga abin tada hankali ba, duk abin da ka yi shi za a yi maka, an ce zina bashi ce, ka yi da matar wani, ƙila shi yasa wani ya so yi da ni, in sha Allah biyan bashinka ba zai taɓa faɗawa kaina ba, sai dai kan ƴaƴanka, waɗanda za ka haifa da matarka ta nan gaba!". Daga haka ta fashe da kuka, ta fice daga wurin cikin sauri kamar za ta kifa. Ali sai ya ji kamar an sare masa ƙafafu, sosai maganganunta suka kashe masa jiki, har mutanen da ke ta ƙoƙarin raba su, suka ja shi suka fitar bakin titi ji yake kamar a mafarki Maryam ta faɗa masa waɗannan maganganun, ya daɗe tsaye a bakin titin kafin ya saita kansa, ya nemi wuri ya zauna a gefe. Lambar Hajiya ya lalubo ya kira ta, ba ta ɗauka ba, tunowa da mijinta yana gida sai bai ƙara kira ba, har zai tashi ya tafi sai ga kiranta ya shigo, yana ɗagawa ya ce"Hajiya me na yi miki da za ki yi mini haka? Me matata ta tsare miki?" Hajiya ta ce"Aliyyu ban gane ba fa, mene ne yake faruwa?" Ali ya ce"Kar ki raina min hankali mana! Ke ce kika sa maza suke ta bibiyar matata, har na fara zarginta, har condom kika aiko mata har gida! Me na yi miki? To daga yau babu ni babu ke har abada, wallahi na yi nadamar saninki Hajiya, na yi nadamar aikata zina". Ya kashe wayar, yana jin raɗaɗi a zuciyarsa. Hajiya ya kira yaron da ya gama yi mata bayanin aiki saura ƙiris, yana ɗauka ta ce"Ya za ka yi mini haka!?" Ya ce"Wallahi Hajiya matsala aka samu..." A zuciye ta katse shi da faɗin"Dalla rufe mini baki, ka san yadda nake son yaron nan kuwa? Ashe kai lusarin banza ne ba ka iya tsara komai ba? Tirr!" Ta kashe wayar tana huci. Babu jimawa mijinta ya shigo ɗakin nata, wani abu da bai saba yi ba, ta tashi da sauri tana murmushin yaƙe ta ce"Alhaji! Ka fito?" Fuskarsa babu annuri ya zauna a bakin gadon da take, a tsanake ya ce"Wane ne Aliyyun nan?" Ai ji ta yi kamar ya buga mata guduma a kai, hankalinta ya tashi, lokaci ɗaya ta firgice ta ce"Aliyyu kuma? Ban san shi ma, me ka ji?" Alhaji ya yi murmushi ya fara tattaɓa wayarsa, sai ga shi ya kunna recording ɗin wayar da ta gama yi yanzu, ya kuma kunna wacce ta yi da Alin, ya ce"Har yanzu kina da ƙwarin gwiwar jayayya ko kuma na yi ta kawo miki shaiduna?" Ta fashe da kukan nadama, tana girgiza kai alamar babu. Ya ce"Zuwaira kin ci amanata, cutarwar da kika yi mini Allah Ya miki! An daɗe ana kawo min maganganu a kanki ina sharewa, saboda ba na son na zarge ki akan ƙarya, da na ga magana ta fara yawa a kanki sai na yi tunani na ga ba ke kaɗai ba ce matata, me yasa kowa shunenki yake yi mini ban da sauran, hakan ya sa duk na biyawa matana Umara ban da ke, saboda na zauna da ke na fuskance ki sosai, tun da na dawo na sa ake kula da shige da ficenki, duk inda kika je a tafin hannuna yake, na kafa ayar tambaya a kan yaron da kika fitar a seal, cikin satin nan kuma na samu dabarar bibiyar wayoyinki, sai ga shi kuwa komai ya bayyana ta sauƙi". Kuka kawai take yi, ganin ya tashi zai fita, ta je ta ruƙo shi ta ce"Don Allah ka rufa min asiri, wallahi na tuba!". Ya fizge ya fita ransa a matuƙar ɓace. Hajiya ta zauna a ƙasa dirshan ta saki gursheƙen kuka, haka ta wuni a ɗaki cikin mummunar fargaba, sai da aka sha ruwa ta fito ta sha ruwa, tana jin saukar zazzaɓi a jikinta, kuma sai karkawa take yi, shayi ta haɗa ta sha rabin kofi don a zatonta karkarwar yunwa ce, duk da cikin nata ma a cushe take jinsa, tana ajiye kofin ta ji mararta ta fara ciwo, ta shiga bandali don yin alwalar magriba ta ga jini, ta gyara jikinta ta kwanta tana ta fargabar matakin da zai ɗauka, tana kuma sauraron ciwon mararta da yake ƙara ƙaimi, can dai ta ji zubar jinin ma ya wuce wanda ta saba, ta jiƙe jaƙab, ta tashi a firgice tana mamaki, ta dinga zarwar shiga banɗaki tana gyara jikinta, da ta ga abun ya yi yawa, ta fice ta tafi asibiti. Aka ba ta gado tare da yi mata gwaje-gwaje, result ya fito, nurse ɗin ta zo tana yi mata bayani"Hajiya cikin jikinki ne ya so zubewa, amma yanzu mun dakatar da abun, in sha Allah babu wata matsala kuma, sai dai za ki daina ayyuka da motsa jiki na..." "Keee!" Tsawar da Hajita ta daka mata, ta sa ta datse bayaninta, ta tashi zaune ta ce"Wace ce mai cikin?" LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/19, 5:29 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Nurse ɗin ta ce"Hajiya kina ɗauke da ciki na wata biyu". Ƙirjinta ya doka da ƙarfi, sai kuma ta rasa wanne za ta ji tsakanin farinciki da baƙinciki, tun da ƙuruciya take fata da mafarkin zuwan wannan ranar, ranar da za ta ɗauki cikin ɗan mutum ta haife shi tana kallon shi a matsayin jininta, magajinta, to ga shi mafarkinta ya tabbata, sai dai abun ya zo a baibai ba ta yadda za ta so ba, zuciyarta ta rabu biyu wani sashe na faɗa mata ta sa a zubar da cikin nan take, yayinda ɗayan sashen ke tuna mata ta daɗe da wannan burin fa, kuma wataƙil shi kaɗai ne rabonta. Tana so ta haihu, sai dai ko ƙaramin yaro ya san cikin jikinta ba na Alhaji ba ne, tana kyautata zaton na Aliyyu ne, wanda bayyanar hakan daidai yake da mutuwar aurenta, wata zuciyar ta faɗa mata ai dama auren dole zai mutu ko da ciki bai bayyana ba, saboda haka gara ma ta bar cikinta, ta haife shi ko da ba su yi aure da Aliyyu ba, ta san ta bar baya, tana da mai yi mata addu'a, da wannan ta fi samun nutsuwa don haka ta saurari bayanin nurse ɗin, ta rubuta mata magunguna, a hanyar komawa gida ta siya. Da ada ne da tuni ta kira Ali a waya ta faɗa masa halin da take ciki, to sanin ana bibiyar wayar tata ne ya sa ta share. Kamar mara laka ta shiga cikin gidan, a falo ta tarar da Alhaji yana duba laptop, da abinci a gabansa. "Daga asibiti nake, zazzaɓi ne ya rufe ni". Ta faɗa kamar ya tambaye ta. Alhaji ya rufe laptop ɗin ya ce"Hakane daga asibiti kike, kuma kin samu albishir kan abin da kika daɗe kina nema, ƙila ma dalilin shi kika fara rabawa maza mutuncinki da igiyar aure a kanki, ina taya ki murna, Allah Ya raba ku lafiya". Tun da ya fara magana take hawaye, ba ta yi mamaki sosai ba, tun da ta san yana bibiyarta, ta duƙa a gabansa ta saka gwiwowi ta sunkuyar da kai ta fara magana"Alhaji tabbas na tafka babban kuskure a rayuwata, na shafawa kaina baƙin fenti, amma ka sani kai ne mai laifin, a kaso ɗari kai kake da saba'in, ka watsar da mu, muna zaune a gida ne kawai muna amsa sunan matan aure, amma marabarmu da marasa auren ƙalilan ce, sai ka yi watanni ba ka waiwayo mu ba, ka bawa nemanka muhimmanci sama da matanka, ko kana nan ɗin ma ya aka cika? Ka sani ba ka da cikakkiyar lafiyar da za ka tsarewa mace ɗaya sha'awarta, amma kana auren mata uku, wannan duka ba cutarwa ba ce?" A tsanake ya ce"Cutarwa ce Zuwaira, amma tun da har kin ga ba za ku jure ba, me ya hana ki nemi rabuwa? Ai shi zaman aure ɗan maslaha ne". Ta share hawaye ta ce"Iyayena ba za su fahimce ni ba, a zamin nan indai namiji yana bawa mace ci da sha, to duk wata nau'in cutarwa da zai yi mata, ya sha, a yadda gidan nan yake da komai na more rayuwa, ban rasa komai ba sai kulawarka da kuma haihuwa, ba kowa ne zai yi mini kallon mai hankali ba idan na yi yunƙurin rabuwa da kai. Ka ɗauke nauyin gidanmu, kai ke yi musu komai, tamkar su suka haife ka, yau idan na je musu da zancen rabuwa da kai kana tunanin ba za su ga wautata ba? Tsufa ya kama su, bai kamata na ɗora musu matsalolina ba, shi yasa na zaɓi na rayu a hakan kawai, sai dai na kasa jurewa tsare kai daga sha'awa ba ƙaramar jarumta ba ce, ni ba jaruma ba ce, na kasa!". Ya yi shiru yana sauraronta, duka maganganunta gaskiya ne, sai dai ban gamsu da hujjojinta ba sam. Ta ce"Duk hukuncin da ka yanke a kaina zan karɓa, kowane bawa da kalar ƙaddararsa". Alhaji ya ce"Hakane, to a gaskiya Zuwaira ba zan iya jure ci gaba da kallonki a matsayin matata ba, ko babu cikin wani a jikinki wallahi ba zan iya zama da ke ba, tun a jiya na rubuta miki takardar saki ɗaya, idan kin shiga ɗakinki za ki tarar da ita a kan mudubi, a sanina kin taɓa siyan gida kika saka ƴan haya, yana nan?" Ta gyaɗa masa kai alamar yana nan. Ya ce"To zan ba ki miliyan ɗaya, sai ki ƙara a jarinki, don ki dogara da kanki, Umma da Baba sun zama iyayena, wannan ba zai canza ba har abada, saboda haka ba zan janye kyautatawata a gare su ba, za ki zubar da cikin ne ko za ki haife shi?" Ta ce"Ba zan sake aikata wani kuskuren ba, ban san me yasa Allah Ya ba ni haihuwa ta wannan ɓangaren ba, saboda haka zan haife shi". Ya jinjina kai ya ce"Kina da zaɓi, ko ki zauna ki gama iddarki a nan, ko ki koma gidanku, ni gobe zan bar gidan, ba don cikin jikinki ba da zan faɗawa iyayenki ba ni da dalilin rabuwa da ke, zama ne ya ƙare, saboda kar asirinki ya tono". Ta ce"Babu komai na gode". Daga haka ta tashi za ta shiga ɗaki, ya karɓi wayarta ya yi danne-danne ya miƙa mata ya ce"Yanzu babu mai bibiyarki kya iya yin wayoyinki a tsanake". Ta gyaɗa kai ta shige ɗaki, ya dafe kansa sa hannu biyu yana cewa"Tabbas zina bashi ce, Astagfirullah! Allah na tuba". Zama ta yi ta riƙe baki hawaye na saukar mata, ta dinga tuna tun farkon aurenta, tun tana ƴar shekara goma sha bakwai ya aure ta, sun yi rayuwa mai cike da nishaɗi, yana da halaye na ƙwarai, rashin ba ta kulawa ne kawai matsalarsa, tun farko a haka suk rayuwa kafin ya ƙara aure abun ya ta'azzara, musamman ma da ya bar zaman garin, sannan ya nuna ba shi da sha'awar tafiya da matarsa, aiki ne ya kai shi, shi zai yi. Ta so ya barta ta yi karatu ta samu aiki, ko hakan zai rage mata kewa, sai ya nuna sam ba shi da ra'ayin wannan, ya ba ta jari tana kasuwancinta ya haɗa ta da ƴan kasuwa suna kawo mata kaya. A baya haƙurin kawai take tana jurewa, kafin ta faɗa ga halaka sanadin shawarar ƙawa da ta nema, wacce matar abokinsa ce da suke yawacen-yawacensu tare da Alhajin, ita ta fara kwaɗaita mata harkar nan ta faɗa mata ita ma haka take yi, nan ta haɗa ta da Reza ta fara yi mata kawalci, har zuwa yau da komai ya faru. Tunani kawai take yadda za ta kalli iyayenta da wannan babban abun kunyar da ta kwaso, da girmanta da shekarunta, sai kuma tunanin yadda Alin, iyayensa da matarsa za su ɗauki lamarin, tana fatan a ce wannan ya yi sanadin rabuwar shi da matarsa, idan ta haihu sai su yi aure, ta ba shi jari ya fara kasuwanci su zauna a gidanta, su raini ɗan da Allah Ya ba su. Washegari da sassafe Alhajinta ya tattara ya bar gidan, ta kira Ali a waya, yana kallon wayar har ta yi kira uku bai ɗauka ba, saboda ya yi wa kansa alƙawarin nesa da zina, a yanzu ya yi nadamar aikata komai, ya shirya fuskantar Maryam don su gyara zamansu, saboda haka ya saka lambar Hajiya a blacklist. Da daddare ya shirya ya tafi gidan su Maryam, duk da akwai zazzaɓi a jikinsa kaɗan, a tsakar gida suka gaisa da Maman Maryam ɗin, ta ce ya shiga ɗaki tana ciki. Tana zaune ya shiga da sallama, ta amsa babu yabo babu fallasa, ya zauna ta gaishe shi ya amsa, duk sai suka yi shiru ya rasa ta inda zai fara, can dai ta ce"Ni na rasa inda zamanmu ya dosa, abubuwa sai faruwa suke yi marasa daɗi, gobe ma ba mu san mene ne zai faru ba". Ya ce"Ki yi haƙuri Maryam, duka ni ne na ja komai, amma ke ma da na ki laifin, na rasa me kika ɗauki rayuwar aure, me yasa kike guje mini? Ni dai na san kina sona, amma sam ba kya so na raɓe ki, hakan da kike yi mini ne ya saka ni a halakar da ta assasa komai, da ba kya guduna wataƙil da tuni muna gidanmu yanzu haka muna rayuwa mai inganci, ki faɗa min dalilinki, ba kya jin daɗin yadda nake mu'amalantarki ne ko kuma ina cutar da ke ta wani fannin?" Ta share hawayen da suka sakko mata, ta ce"Ba na so har zuciyata, bana fahimtar komai a ciki sai wahala, shi yasa ba na so, sam ba na jin ko ɗugun sha'awar namiji". Ya sauke ajiyar zuciya ya ce"Tabbas akwai mutanen da Allah Ya ke halittarsu a haka, maza da matan, amma ƙalilan ne, wasu da yawa cuta ce a tare da su ta haddasa musu wannan, cuta ko ta cikin jiki ko ta shafar jinnu, don haka dole ne mu bincika mu san matsalarki, Maryam ina so mu gyara gidanmu". A sanyaye ta ce"To zan yi magana da yayata, sai na ji shawararta, duk yadda muka yi zan faɗa maka". Ya ce"Allah Ya sa na ji alkhairi! Ina ƙaunarki Maryam, don Allah mu yafewa juna laifuka". Ta ce"Ba na riƙe kowa ballantana kuma kai da kake mijina, na yafe maka duk laifukan da ka yi mini na baɗini da na zahiri". Ya yi murmushi ya ce"Ai dama masu masifa irinki ba sa ruƙo, lokaci ɗaya kuke yi ku gama. Maryam ni ma na yafe miki komai, Allah Ya haskaka rayuwar aurenmu". Ta amsa da Amin, daga nan suka shiga fira, ya yi mata zancen zai kama haya su tare, ta ce ya bari sai bayan sallah, kafin lokacin ta nemi magani, suka rabu a kan haka. Washegari ta je gidan yayarta, ta cire kunya ta faɗa mata komai, ta yi mata tambayoyi nan ta gane ciwon sanyi ya yi mata katutu, ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Gaskiya Maryam sanyi ne ya yi miki illa, ya zama dole ki tashi tsaye ki nemi magani. Akwai ingantaccen maganin sanyin mara da nake amfani da shi, na BOJUWA HERBAL'S & SCENTS, wata marubuciya ce mai siyarwa sunanta Surayya Dee, ina kyautata zaton idan kika yi amfani da shi za ki dace, zai wanke miki mara tass, wataƙil ma sanyin ne ya kawo miki rashin haihuwa, a yau zan saka order in sha Allah gobe har gida zan kawo miki, ki fara amfani da shi, cikin kwana uku kacal za ki ga aikinsa". Maryam ta yi mata godiya, suka yi sallama ta tafi. Da yamma Aliyyu yana zaune a ƙofar gida, waya yake da Maryam tana faɗa masa yadda suka yi da yayarta a kan matsalarta, kwatsam ya hango Reza tana tunkaro shi ita da wata mace mai ɗauke da hijjabi da niƙabi, da sauri ya yi wa Maryam sallama, ya miƙe tsaye tun kafin su ƙaraso. Reza ta ce"Yawwa ni na sauke nauyi, Hajiya ga ki ga Ali, ku gama lafiya" Ta juya ta tafi. Hajiya ta ɗage niƙab ta ce"Haba Aliyyu ya zan ta kiranka ka ƙi ɗauka, ƙarshe ma ka yi block ɗina?" Ali ya ce"Yanzu Hajiya don Allah me yasa za ki biyo ni har gidan iyayena? Ni fa na tuba, babu wata mace da za ta sake yaudarata wallahi!". Hajiya ta sauke numfashi ta ce"Ni ma ai na tuba Aliyyu, yanzu ko da kuɗi ba zan aikata zina ba, babban dalili ne ya kawo ni wurinka, ya kamata ka san ko da mun rabu, akwai sauran alaƙa, Aliyyu a yanzu haka ina ɗauke da ciki na wata biyu, kuma a bincike na, kai ne uban cikin nan, aurena ya mutu sanadinka, amma duk da haka na ɗauki ƙaddara zan haifi ɗanmu, don haka na zo na sanar maka mu san yadda za a yi, yana da kyau manyanmu su sani". "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Allahumma ajirni fi musibaty wa aklifni khairan minha" Ali ya furta yana jin kamar zuciyarsa tana tarwatsewa saboda tashin hankali. Bai gama dawowa daga shoke ba ya ga Hajiya ta saka kai cikin gidan nasu, kafin ya yi wani yunƙuri har ta fara rafka sallama, sai ya kasa bin bayanta, ya zauna dabar akan dandamin ƙofar gidan, yana fatan Allah Ya sa mafarki yake yi. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/22, 4:13 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 Mahaifiyar Ali ta fito tana amsa sallamar ta ce"Lale, ƙaraso". Ta shimfiɗa mata tabarma ta zauna, tana kallon Ali da ya yi musu tsaye fuska kamar hadari, ta ce"Kai kuma lafiya?" Hajiya ta yi murmushi ta ce"Ai zama zai yi, maganar tashi ce". Ali ya janyo kujera ƴar tsuguno ya zauna, bayan an gaisa Hajiya ta kwashe komai tun daga kan haɗuwarsu da Ali har yako yanzu ta faɗawa mahaifiyarsa, Umma ta kalli Ali kamar za ta yi kuka ta ce"Yanzu dama Ali irin rayuwar da kake yi kenan? Da aurenka da komai kake tsallake matarka, kana bin matan banza, har da matar aure ma? Ali da gaske cikin nan naka ne?" Ya ce"Umma wannan kuma Allah ne ya san gaskiya". Ta kai masa duka da mafucin kusa da ita, ta ce"Haka ma za ka ce mini? Duk abubuwan da ta faɗa gaskiya ne ka aikata kenan!". Hajiya Zuwaira ta ce"Ki yi haƙuri Umma, kowane bawa da kalar ƙaddararsa, wannan shi ne tamu ƙaddarar ni da Aliyyu..." A fusace Umma ta ce"Ke dalla can rufe mini baki, babbar banza kawai babbar kwabo wacce ba ta san darajar aure ba! Ke har kina da bakin faɗin ƙaddara? Da aurenki da komai ki dinga gayyatar yara gidanki? Allah Ya isa tsakanina da ke" Sai ta fara kuka, ta tashi ta rufe Ali da duka, ganin kamar ma ita ce take jin zafin a hannunta shi ko a jikinsa ta koma ta zauna, tana kukanta. Hajiya ta ce"Umma kina da ikon faɗin komai, tun da dole na san za ki shiga damuwa, kamar yadda na faɗa mu bar hakan a ƙaddara, ni ba zan zubar da cikin jikina ba..." "Saboda me!?" Umma ta tambaye ta a razane. Hajiya ta zayyano mata duka tarihin rayuwarta ta gidan Alhaji, ta ɗora da faɗin"A yadda girma ya fara kama ni, na kusa wuce shekarun haihuwa, ƙila idan na zubar da cikin nan shi kenan ba zan sake samun wani ba, haka zan yi yankakken baya". Umma ta ce"Ai kuwa haihuwar nan ba za ta yiwu ba, tun da yana da mata, wannan ba ƙaramar fitina zai haifar ba, sannan me za mu ce da duniya?" Hajiya ta ce"Umma ni ba na gudun bakin duniya, don mutanen duniya ba ka taɓa iya musu, yanzu haka zan je na sanarwa iyayena, duk yadda muka yanke za ku ji, idan Ali yana so na bayan na haihu sai ya aure ni, idan ba ya so na babu komai, zan ba shi ɗansa ko ƴarsa". Ta tashi ta fice, Ali ya bi bayanta da sauri, a zaure suka tsaya, ya ce"Hajiya don girman zatin Allah ki cire cikin nan, ki rufa mini asiri, ban san amsar da zan bawa matata ba". Ta ce"Aliyyu kenan, haka ni ma ban san amsar da zan bawa Allah ba idan na cire kyautar da ya ba ni". Daga haka ta wuce ba ta sake sauraronsa ba. Ɗan ƙaramin yaƙi aka yi a gidan iyayenta, don sai da ta tara duk ƴan'uwanta na jini sannan ta zube musu labari, da yawansu mutuwar auren ta fi damunsu fiye da cikin, saboda alkhairin Alhaji a gare su. Kuma abun takaici Hajiyar sam ba ta damu da cikin ba, sai ma ƙoƙarin nusar da su da take yi, kan ta daɗe fa tana nema, sai yanzu Allah Ya bata, saboda haka ba za ta zubar ba, mahaifinta kam ƙarshe cewa ya yi ba za ta zauna a gidansa da cikin shege ba, ita ba yarinya ballantana a dake ta, kuma duk suka ƙi karɓar maganarta da ta ce su zo a je gidan iyayen Alin. Ita dai nata ba su haƙuri kawai, ba ta da cikakkiyar lafiya, kuma a yanayin rashin lafiyar cikinta zirga-zirga da hayaniya ko tashin hankali duka ba nata ba ne, shi yasa ta yankewa kanta hukuncin komawa gidanta, cikin zuciyarta tana ta shawarwari, ta kira Alhaji ya ɗauka kamar ba a yi komai, ta faɗa masa duk yadda suka yi da iyayenta, ya ce"To wannan ai tsakaninku ne, ni akwai nawa a ciki?" Ta ce"Babu, alfarma nake so ka yi mini don Allah, ina so na ci gaba da zama a nan gidan naka har zuwa lokacin da zan haihu". Ya ce"Wannan ai babu damuwa, dama kuma ai na ba ki zaɓi da hakan, Allah Ya raba lafiya" Daga haka ya ajiye wayar. ALI A ranar sallah da yamma babu zato sai ga kiran Salma, ta ce ya zo tana son ganin shi, ta yi masa kwatance, ya tashi ya tafi, ɗan ƙaramin gida kwatancen ya kai shi, ya ƙwanƙwasa babu jimawa sai gata ta fito, suka gaisa, ya ce"Allah Ya sa dai lafiya". Ta ce"Lafiya ƙalau Aliyyu. Wallahi ina ta tausayinka ne har yanzu, Alhaji ya cuce ka fa, amma ba ka haƙura ba ka ɗauki wani mataki ba". Ali ya ce"Babu komai, Allah zai mayar da alkhairi". Ta ce"Yanzu wane aikin kake yi? Kuma ka samu gidan?" Ya girgiza mata kai kafin ya ce"Ina ta duba aikin dai, kin ga aikin gwamnati yanzu ba abun ka tsaya ɓata lokacin wurin nemansa ba ne, to sana'ar hannun ma wallahi sai ka wuni kana garari ba ka samu ba, ga azumi, shiyasa na tattara komai na jingine sai bayan sallah. Gida kuma na samu wani, yau na ciki za su tashi, jibi za mu tare in sha Allah". Salma ta ce"Ayya! Ai da cewa zan yi ku zo mu yi zamanmu a nan. Ka san auren ya mutu, babana ya kasa fahimtata, saboda Alhaji yana kyautata masa, duk da ya ji komai ya kuma tabbatar amma yake cewa dole na yi haƙuri na ci gaba da zama a ɗakina, sai Farha ta bar gidan, da na nuna ban amince ba, har ma na yi yunƙurin zuwa Hizba na nemi haƙƙina, sai ya sake ni, don kar asirinsa ya tonu, shi kuma Baba ya ce kar na sake na doso gidansa. Wannan gidana ne, da na mallaka da aikina, ɗakuna huɗu ne a ciki, ciki da falo guda biyu, sai kitchen da banɗaki, ba na jin daɗin zama ni kaɗai ɗin ina mace, na so ku zo mu zauna, tun da ni ina gama iddata ma wani auren zan yi in sha Allah!". Aliyyu ya ce"Allah Ya yi miki sakayya, Ya sa hakan shi ne alkhairi a gare ki, a gaskiya ba na jin za mu zauna, tun da na riga na kama wani zai fi kawai, Maryam tana da kishi, shi yasa ma sam ba na son abin da zai sa mu zauna a gida ba mu biyu ba". Salma ta ce"Allah Ya ƙara muku zaman lafiya. An ce a da kafinta kake yi ko?" Ya gyaɗa mata kai Ta ce"To akwai wani abokin aikina, da yake da wani babban wuri, suna yin irin sana'ar taku, suna kuma shigo da kayan waje, na yi masa zancenka, ya ce zai ba ka gurbin aiki, shi ne na ce bari na ji ta bakinka". Ali cikin farinciki ya ce"A ina so mana, na gode sosai Allah Ya saka da alkhairi". Salma ta ce"Babu komai Aliyyu, bari na ba ka lambar shi, ka faɗa masa ni ce na turo ka". Ta ba shi lamba suka rabu, a ranar ya kira shi, ya yi masa kwatancen wurin, washegari da sassafe ya tafi wurin, suka daidaita komai, suka tsaya a kan sallah da kwana uku zai fara zuwa, ranar da za su koma aiki. Da daddare ya je gidansu Maryam da take ta shirye-shiryen tarewarsu, tana kuma ganin kyaun maganin sanyin da take ta amfani da shi, sosai take shiri don ta ɗaura ɗamarar sake halayenta, za ta buɗe shafin kyautata masa ta dinga ba shi haƙƙinsa ko da kuwa ba ta so. Bayan sun gaisa Ali ya faɗa mata aikin da ya samu, ta taya shi murna, don dama sosai zamansa haka ya dame ta, ko da wasa bai yi mata zancen Hajiya da cikin jikinta ba, saboda ba ya son abin da zai wargaza yarda da zaman lafiya da ya suke ƙoƙarin ginawa a rayuwar auren tasu. Sun tare a gidansu, kamar wancen haka wannan ma yake, ɗaki biyu, kitchen da banɗaki, iyayenta sun siya mata katifa, ƴan'uwa sun haɗa mata kuɗi da kayan sakawa, sababbi da kwance, shi ma Ali ya ba ta kuɗin duk ta haɗa ta yi siyayyar abubuwa masu muhimmanci da dole za su buƙata. A bisa shawarar da suka yanke sai ta gama amfani da magungunanta sannan su gwada su ga ko ta samu lafiya, don haka bai bi ta kanta ba, suka fara gudanar da rayuwarsu cikin aminci, musamman ma da ya ga Hajiya ba ta sake nemansa ba. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/22, 4:13 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 A hankali sakanni suke juyawa su bada mintuna, su ma su juya su bada awanni, awanni su samar da kwanani, yayinda kwanaki ke rikiɗa su bada shekarun da za su zama ƙarni guda. Abubuwa da dama sun faru a cikin watanni biyar da suka wuce. HALIMA Wata ɗaya da zubewar cikin jikinta, Aisha ta zauna da mijinta ta nuna masa sha'awarta na son auren shi da Halima, sosai ya yi mamaki saboda ya fi kowa sanin kishinta, ya kalle ta sosai don ya gane tana cikin hayyacinta ko sambatu take yi, ya ce"Aisha da gaske kin san abin da kike faɗa kuwa?" Ta ce"Ƙwarai kuwa, ga shi na maimaita maka ma, ina so ka auri ƙanwata Halima, kuma auren ya kasance cikin ƙanƙanin lokaci ma". Ya ce"Amma dai gaskiya na yi mamaki sosai, a zatona idan na tashi yin aure sai an kai ruwa rana da ke, sai ga shi wai yau ke ce ma kike nema na yi. Aisha zan yi aure, amma ba zan iya auren ƴar'uwarki ba, a ganina sai ya fi taɓa zuciya, gara dai na samu wata can a waje". Ta yi saurin girgiza kai ta ce"A taka fahimtar kenan, ni kuwa duniya babu wacce za ka aura mu zauna lafiya sama da Halima, sai da na zaɓo ta na rairaye, Halima aya ce guda ɗaya a cikin buhun tsakuwa, idan na rasa ta a matsayin kishiya, ba za ka taɓa auro wacce nake so ba, ita ce za ta dace da rayuwarmu". Ya sauke ajiyar zuciya ya ce"Amma kin yi magana da ita, ta ce tana so na? Sannan ni ma ban san ta inda zan fara tunkararta ba". Ta yi murmushi ta ce"Maza kenan, wato ba ka san ta inda za ka fara ba ko? Kafin a kwana biyu ku dinga shigewa ɗaki ina jin shiru. Ka bar komai a hannuna, kawai idan lokacin da ya dace ka shiga maganar ya yi, zan neme ka". Ya yi murmushi suka bar maganar. Sosai aka hau tudu da gangare kafin Halima da sauran ƴan'uwa su yarda da auren, ganin Aishar ce ma take ta shigewa gaba ne ya sa aka samu sassaucin lamarin, dududu wata biyu kenan da mutuwar aurenta aka ɗaura mata wani auren da mijin Aisha, babu wata shaƙuwa a tsakaninsu, zuwan shi ɗaya tun da ta baro gidan, sai dai kullum yana kiranta a waya sau ɗaya suna gaisawa, Aishar ce ta karɓi kuɗi a hannunsa ta yi wa Halima komai na hidima, har da kayan ɗaki, ya so a ce ya raba musu gida amma ta kafe a kan ita dai tare za su zauna. Haka aka kawo Halima tun tana ɗari-ɗari da Alhaji har ta fara sakin jikinta, sai dai da yake dama can ita ba mai rawar kai ba ce har yanzu da take ɗauke da cikin wata uku shaƙuwarsu ba ta kai ta kawo ba. Shi dai yana jin sonta sosai a ƙasan zuciyarsa, saboda kyawawan halayenta, uwa-uba kuma ga shi zai samu cikar burinsa na haihuwa daga gare ta, sannan suna zaman lafiya da Aisha, ba ta taɓa kawo ƙorafi akan ƙarin auren ba. Ɗaki ɗaya aka bata, ya zamana falo na kowa ne, to ita har yanzu ba ta ma wani zaman falon, ji take ɗakin ma ya ishe ta, don har yanzu akwai ɓurɓushin jin kunyar Antin tata a idonta, kitchen ma duk da kayan Aishar suke amfani, tare suke aikin komai da ƴar aikin gidan, wacce suka yi sabo sosai, don ko da aka yi auren babu wani abu na gyaran jiki da aka yi wa Halima, kuma Aisha ce ta hana ta ce ita za ta yi, sai dai ganin har an yi aure da sati ɗaya ta yi ƙirmisisi babu niyyar za ta bata ko ƴar zuma ya sa Halima ta tambayi wannan ƴar aikin ko ta san inda ake siyarwa, ta ce wata a unguwarsu tana siyarwa, nan Halima ta bada kuɗi a cikin sadakinta aka haɗo mata bridal package na BOJUWA HERBAL'S, ta yi amfani da su a ɓoye, kuma ta ga ingancinsu sosai. Zamansu da Aisha kadaran-kadahan ne, don dama can shaƙuwar ba sosai ba ne, don ita idan ta raina ajin mutum bai kai ta tsaya fira da shi ba, ballantana yanzu da take kishiyarta, sai da daina janta a jiki ta daina sakar mata fuska, ita dai Halima ba ta wani damuwa, tun da shi mijin yana ta ƙoƙarin ganin sun zama abu ɗaya, kuma yana kyautata mata, ta ci abin da ranta yake so, ta kwanta a cikin AC. Gefe guda kuma ƴan'uwan mijin suna ta ƙoƙarin janta a jiki, musamman da ta samu cikin nan, mahaifiyarsa ta ce duk abin da take so ta dinga faɗa ana kawo mata, amma saboda kara irin ta Halima ba ta taɓa faɗar komai ba, sai dai idan aka kwana biyu ta zo da kanta ta kawo mata kayan ƙwalam na gargajiya, ko ta yo mata tuwo, ta dako mata garin yaji, sam hakan ba ya damun Aisha, saboda duka ta raina class ɗinsu har uwar tashi, kallon su kawai take yi. Halima ta samu nutsuwa ji take ko a iya wannan ta tsaya ai ta samu canjin rayuwa daga ƙuncin gidan Haruna. GIDAN HARUNA Tun cikin azumin Zainab ta zubar da cikin, bayan sallah aka ɗaura musu aure, tana farinciki da auren sosai saɓanin Haruna da bai san taƙamaiman abin da yake ji ba. Wannan auren shi ne ya sama mata ƴanci ya bata lasisin ci gaba da neman kuɗinta, ta hanyar maza, ƙarya ta yi masa ta ce za ta fara siyar da magungunan mata, idan ya tafi kasuwa ita ma sai ta fice, da jakarta ta magani, wanda ita take shan abunta, yau su haɗu da wannan gobe su haɗu da wancen, tana adana kuɗaɗenta, ba tare da Haruna ya taɓa kawo haka a ransa ba, tun da ya ga iya ƙoƙarinsa akan hidimar gida yana yi, ita bai isa ya hana ta ko kuɗin maga ba, yanzu za ta fara yi maza zabure-zabure tana cewa a gidan wa yake so ta sato? A dole yake kawo mata komai na buƙata. GIDAN ALI Sosai aka samu canji, zaman lafiya, kwanciyar hankali da soyayya, Maryam ta warke tsaf daga wannan cutar da ciwon sanyi ya saka mata, a yanzu wataran da kanta ma take neman mijinta, tun Ali yana mamaki yana yi mata dariya har ya saba. Yanzu haka tana da ciki na wata biyu. Ali yana samu sosai a sabon wurin aikin da yake zuwa. Wata biyar kenan bai san halin da Hajiya take ciki ba, duk a zaton shi ta zubar da cikin ta tafi harkokinta, ko ma ta samu miji ta yi wani auren, kwatsam yau yana zaune tare da Maryam da daddare sai ga kira daga mahaifiyarsa, suka gaisa, muryarta da damuwa ta faɗa masa ga wannan Hajiya ta zo fa, tana son a tattauba, ƙirjinsa ya doka da ƙarfi, ya fara furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Maryam tana tambayarsa abin da yake faruwa ya ce Umma ce babu lafiya, ya zura jallabiya ya fice. A tsakar gida ya tarar da Hajiya zaune shirim kamar kayan wanki, ta ƙara ƙiba sosai, cikin jikinta ya fito kamar ƙwarya, ya ji jiri yana son ɗibarsa, ya dafa bango yana hasbunallahu wa ni'imal wakil, kamar zai yi kuka ya ce"Wai Hajiya me kike nufi da ni?" Ta ce"Me kake nufi da ni dai! Zuwa na yi don ku gan ni ku tuna da jininku da yake shirin zuwa, yau da na je scanning aka ce ƴan biyu ne mace da namiji, shiyasa na zo faɗa maka don ka shirya, daga yau zuwa sati ɗaya, idan ba ka zo mun daidata ba, zan kaika Hizba su ƙwatar mini haƙƙina dake kanka, ga lambata nan da adress!" Ta wurga masa takarda, ta fice. YUSRA Tana kammala idarta maza suka fara sako kai, sai dai babbar damuwarta duka babu saurayi, sai masu aure, ga shi tana son yin auren ko don takurar da Babanta yake yi mata, da kuma son nunawa Sadiq ba fa shi kaɗai ne namiji ba. Don haka ta haƙura ta auri wani mutumi, duk da ba wani son shi take ba, matarsa ɗaya da ƴaƴa huɗu. Shi dai yana nuna mata soyayya sosai, gidansu ɗaya da kishiyar, babban falo ne na kowa da kowa, mai ɗauke da kitchen wanda shi ma na haɗaka ne, sai kuma ɓangaren kowaccensu, ƙaramin falo da ɗakuna biyu a ciki da bandaɗi. Babban ƙalubalen da ya fara fuskanta shi ne, ya ce shi a tsarinsa yadda ake raba kwana haka za a raba girki, duk ranar kwananka kai ne za ka yi girgi daga safe zuwa dare, kowa ya ci, babu zancen raba girki, ya ce babu ruwan shi da aikinta matuƙar tana sauke duk nauyinta na hidimar gida. Sosai hakan ya saka Yusra a damuwa, idan tana da aikin safe, tun ƙarfe uku na dare take tashi ta fara haɗa abin da za su ci, kafin ya bar gidan sai ta yi har girkin rana ta ajiye, ta gyara duka gidan, a hakan ma kishiyar tata ta yi ta masifa tana cewa abinci yana sandarewa a kula. Idan aikin dare ne da ita haka za ta yi girki da la'asar kafin ta tafi, sai ya tsiri cewa shi ba ya son abinci a kula, ya fi so ana saukewa a zubo masa, ga shi sai an yi sallar isha'i yake dawowa gidan, haka ta haƙura take yi, sai kuma ya fito da sabon salon tana gama girki bayan isha'in zai ce to ta sallame shi kafin ta tafi ta bar shi da kewarta, sai ya zama kowa a wurin aiki ya gane kullum a latti take zuwa, aka fara yi mata ƙorafi, Sumayya da kanta ta je ta kai tsegumi wurin manyansu, aka shatawa Yusra babban layi a kan hakan, ta shiga damuwa sosai saboda barazanar rasa aikinta wanda take jinsa saƙale da rayuwarta, ta yi wa mijinta bayani ya ce shi dai ita ya aura ba aikinta ba, bai ga dalilin da zai sa ta ƙi kula da gida saboda aiki ba, idan ta ga za ta samo ƴar aiki ta dinga biyanta wannan bai dame shi ba. A yanzu kam ta tsani ko jin kalmar ƴar aiki, hakan ya sa ta roƙi yayarta ta bata ƴarta wacce ta gama secondary, ba ta ci gaba da karatun ba, kuma babu wani tsayayyen miji, aka ba ta Na'ima, take yi mata aikace-aikacen, sai a lokacin ta samu nutsuwa, kafin ya dawo da daddare indai aikin kwana take yi sai ta yi sauri ta tafi. Sai kuma ga shigar yaron ciki a jikinta, wanda laulayi yake son kwantar da ita tana dannewa. Watarana har ta tafi wurin aiki, zazzaɓi ya rufe ta wajen goma na dare ta dawo gida, don ta sha magani ta kwanta, shiru ta ji falon a nan ta yar da jakarta da mayafin, ta shiga kitchen ta zuba abinci kaɗan ta ci, ta yi ɗaki don ɗakko maganin, tana shiga ta ja burki tare da sakin ƙaran da har mararta sai da ta amsa, cike da tashin hankali take kallon mijinta da ƴar yayarta uwa ɗaya uba ɗaya, akan gadonta tamkar ma'aurata. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un! Yau na shiga uku!" Ta furta tana fashewa da kuka. LITTAFIN WANI AUREN NA KUƊI NE A KAN NAIRA 300 KACAL! 8028966015 Sadiya Abdulrazaƙ Opay bank KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN 08028966015 KO KATIN MTN NA 300 ƳAN NIGER ZA KU TURO 300F AIRTEL [8/22, 4:13 PM] Sadiya Abdulrazak: BOJUWA HERBAL'S & SCENTS* *Suna kawo Saiwowin sanyi da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.* *Haka nan akwai dafaffen maganin ga wanda tafi son ready made.* *Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah* *Saiwowin tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru* *Saiwowin matsi gangariya* *Original gadalin mata* *Ƴaƴan gadali na asali* *Original gumba* *Tsumin Saiwowi* *Tsumin kwakwa da Dabino* *Igiyar alkairi* *Zumar goran tula* *Hakkin daka na musamman na asali* *Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*. *Akwai bridal package* *Mai jego package* *Ƴar gata package*. *Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.* *A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne* *Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi* *08032773332* *Serious buyers pls* *Iyah Basiru na gaisuwa*😅 YUSRA Da sauri ta fice daga ɗakin, ta ɗora hannu aka tana jin kamar ta kurma ihu mutane su zo su gani, sai kuma ta sauke hannun ta yi kitchen a guje, wuƙa ta zaro ta dawo ɗakin kamar mahaukaciya tana huci, ta tunkari mijinta da yake saka kaya, a firgice ya yi kan gadon da yarinyar take a rakuɓe ita ma tana saka kayan, yana faɗin"Ke Yusra mene ne haka? Ba ki da hankali ashe!". Tana hargagi ta ce"E ba ni da hankali tun da har na aure ka, ba tare da sanin kai bunsuru ba ne, a cikin ɗakin aurena kake lalata ƴata!? Wallahi gara na kashe ku duka idan ya so a kulle ni har ƙarshen rayuwata!" Ta yi kan gadon a haukace, tsalle ɗaya ya yi, ya murɗe ta ya ƙwace wuƙar, har ta yanki hannunsa jini yana zuba, ya ce"Wannan haukan ba mafitarki ba ce, idan kin ɗaga murya duniya ta jiyo ki, an san mijinki ya yi zina riba kika ci? Idan an ji ƴar yayarki ta yi zina riba kika ci ki ɓata mata suna? Yusra ni fa a zatona kin kawo yarinyar nan ne saboda ta dinga taimaka miki da wasu nauye-nauyen na hakkina dake kanki, kin tafi aiki kin bar ni, ni ɗaya, idan na so kasancewa da ke ya zan yi kenan? Wallahi matsuwa ce ta sa yau ɗin tsautsayi ya kwashe ni na kira ta, amma bai taɓa faruwa ba, ki yi haƙuri". Kamar mutum-mutumi haka ta daskare tana kallon shi, da sauraron maganganunsa da suka azabtar da zuciyarsa, jin shiru ba ta yi magana ba ya sa shi cewa"A gaskiya Yusra ni mutum ne mai yawan buƙatuwa, aikinki ba zai zama uzurin bari na da kewa ba, saboda haka ki zaɓi ɗaya, ko dai aurenki ko kuma aikinki!". A fusace ta ce"Kai a cikin daƙiƙan ma lamba ɗaya ne wallahi! Kai da a tunaninka har zan sake kwana a gidan nan? Kai har ka samu bakin ba ni zaɓi? Wallahi wannan abin da ka yi ba ka ci bulus ba, don kuwa dole sai na saka an ɗaureka har igiya ta yi rara!". "Ni za ki ɗaure!?" Ya tambaya a fusace, yana mamaki. Ta kasa cewa komai saboda takaici, kawai ta buga tsaki ta bar ɗakin, ta koma falo ta zauna, can ta ga fitowar yarinyar ta shige ɗakin da take kwana a ciki da gudu, Yusra ta je ta murɗa ƙofar ɗakin ta ji ta a rufe ƙam, alamar ta saka key, ta yi ƙwafa, ta shiga ɗakin nata, yana zaune a bakin gado, kallo ɗaya ta yi masa ta shige ta fara binciko muhimman abubuwanta, tana zubawa a ƙaramin akwati, sai da ta gama tsaf, ta saka hijjabi kawai ta ji furucinsa "Ke ina za ki je!?" Ko juyowa ba ta yi ba, ballantana ta amsa, ya ce"Idan kika fita daga cikin gidan nan yau a bakin aurenki!" Ta juyo ta yi masa mugun kallo, ta ce"Ya rage naka ka yanke saki nawa kake nufi!" Ta saka kai ta fice, ya biyo ta har tsakar gida, yana kallon sanda ta cire sakata ta fice, ya koma ciki ya zauna a tsakar gidan yana dafe kansa. Wannan ne karo na biyu da aka kama shi da irin haka a cikin gidansa, shekaru biyu da suka wuce matarsa ta taɓa kama shi da ƴar aikinta muraran, wanda ita ba ma kwana ta taɓa yi a gidan ba, da safe take zuwa ta tafi da yamma, watarana ta barta tana aiki ta je unguwa, kafin ta dawo ya dawo gidan, sai zuwa ta yi ta tarar da mugun gani, ita ma a lokacin da ta zuciya za ta tafi gidansu haka ya ce mata idan ta fita a bakin aurenta, ita sai ta ƙi fitar ta kira mahaifiyar shi ta sanar mata komai, ita ta zo ta taushe ta da ban haƙuri har ta haƙura, ga shi har yanzu suna zaune ƙalau ko tashin zancen babu. Yusra tafiya kawai take tana wulla ƙafarta duk inda ta samu, wani irin dunƙulallen abu ya yi ƙabe-ƙabe a ƙirjinta, gefe guda kuma tana fargabar komawa gida, saboda ba ta san me za ta ce ba idan aka tambaye ta dalilin dawowar tata a yanzu, sannan ina Farida ƴar ruƙonta? Anya kuwa za ta iya kallon iyayenta ta faɗa musu mijinta ya lalata yarinyar kuma ya sake ta duka a yau ɗin? Da wane idon za ta kalli iyayen yarinyar? Wannan tunanin ne ya sa ta kasa shiga gidan, maƙotansu ta ƙwanƙwasa ta bada ajiyar akwatinta, ta wuce asibiti, a ƙafa ma ta je duk da akwai tafiya, a chamest ta tsaya ta sayi maganin da zuciyarta ta ɗarsa mata shi ya dace da ita a daidai wannan lokacin, sannan ta shiga asibitin. Da safe ma sai ƙarfe takwas ta koma gida, tana zaton zuwa yanzu sun ji komai, tun da a hasashenta Farida ba za ta kwana a gidanta ba, dole za ta tafi gidansu ko gidan iyayenta. Tana shiga ta tarar da Ummanta a tsakar gida tana wanke-wanke, ta gaisheta, ta wuce ɗaki, tana shiga ta ɗauki ruwa ta sha maganin ta yi kwanciyarta, lokaci ɗaya aka shiga hasko mata mummunan hoton da ta gani a daren jiya, wanda ba za ta taɓa mantawa da shi ba har ƙarshen numfashinta, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ta furta tana runtse ido, zafafan hawaye suka zubo mata, ta daɗe a kwancen sannan ta ji shigowar Umma, ta amsa sallamar da ta yi wasu hawayen na zubowa, Umma ta zauna a tsanake ta ce"Yusra lafiya kuwa? Mene ne ya kawo ki gidan nan da sassafe, kuma ga shi kin kwanta kina kuka?" Ta ce"Umma ki kira Anti Fati ki tambaye ta ko Farida ta koma gida". Umma ta dafe ƙirji ta rafka salati ta ce"Me ya samu Faridan? Ina ta tafi?" Kamar wacce take jira ta fashe da kuka zuciyarta na ƙuna, ta faɗawa Umma komai da ya faru. Umma ta miƙe tsaye tana ta salati ta ce"Lallai Yusra ba ki da hankali, shi ne kuma kika baro ta a gidan? Ya ƙarasata kenan ko?" Ta fice tana ta salati, kamar ana jiran barin Umma gidan, marar Yusra ta fara kartawa, ciwo ya turnuƙeta lokaci ɗaya, sannan ta fara zubar da jini, ta shiryawa komai don haka ba ta wani damu ba, sai ma dama-dama da take ji a ranta, tun da ta tabbata a yau za ta gama iddarta, ta tashi daga matar wannan ɗan bunsurun har abada. To Farida dai a gidan Yusra ta kwana, mijin Yusra yana ta kwantar mata da hankali, da sassafe ya bata kuɗi ta haɗa kayanta, ba ta wuce ko'ina ba, sai can ƙauyensu wanda tafiyar ta kai ta awa ɗaya, nan ta je gidan kakarta ta wajen uba da sunan ziyara ta zo. Babu wanda hankalinsa bai tashi ba da jin wannan mummunan labarin, nan take mahaifin Farida ya sa aka je har gida aka kama mijin Yusra, duk dukan da aka yi masa saboda ya faɗi inda ya kai Farida ya ƙi amsawa, saboda tsakaninsa da Allah bai san inda ta tafin ba, haka aka dinga bin gidajen ƴan'uwa ana kiraye-kirayen waya, sai dare aka gano inda take, ba a bari sai gobe ba aka ɗakkota. Bayan zurfafa bincike a kanta, suka samu ashe ma ba mijin Yusra ne farkon lalata ta ba, dama can ta saba, tun kafin ta gama secondary wani saurayinta ɗan unguwa ya yaudare ta, bayan shi ma ta faɗo maza uku, da aka duba aka ga duk harkar tonon asiri ce, kawai sai aka saki mijin Yusra, kuma a daren ya tura mata saƙo wai ya mayar da aurenta, kiransa ta yi a waya ta dinga surfa masa ashar, har wanda ba ta taɓa jin irinsa ba, kawai a lokacin ɓacin rai ya koya mata su, sannan ta faɗa masa ta gama iddarta, sakamakon zubewar cikin jikinta. Da yake ba shi da kunya har gida ya zo ya nemi ƙarin bayani daga wurin mahaifinta, ya tabbatar masa da faruwar hakan cikin fusata, don a yadda Yusra ta nuna kamar baƙincikin abin da ya faru ne ya yi silar zubewar cikin, haka ya koma gida cike da nadama, don yana son Yusra, kuma ita kanta Farida bai shirya rabuwa da ita a daidai wannan lokacin ba, shi ji yake da za a ba shi aurenta ma tsaf zai yi wuf da ita. Watan Yusra ɗaya a gida, duk ta rame ta shiga damuwa, sosai take nadamar barinta gidan Sadiq, sai a yanzu ta fahimci wauta da asarar da ta tafka, saboda kishiya ta zaɓi rabuwa da shi da ƴaƴanta, kuma ga shi dai sai da ta rayu da kishiyar, ta rabu da mijinta mai halaye masu kyau ta auri mai halin banza, ta rabu da mijinta mai yi mata uzuri akan aikinta, ta auri wanda bai yi mata uzuri ba, babu zato ta ji a duniya babu namijin da take so da burin ƙara rayuwa da shi sama da Sadiq, tana ji a ranta za ta iya komawa aurensa ko da za ta zauna da Kursum a matsayin kishiya, idan ba shi ɗin ba ma ba ta jin za ta sake yin wani auren, don ba ta san wanda za ta kwaso ba kuma. Tun da ta yi aure dama duk sati sai an kawo mata yaranta sun wuni ranar Juma'a, idan kuma tana aiki a ranar sai a kawo su Asabar ko Lahadi, to a yanzun ma da ta dawo gida ba a fasa kawo su ba, su da kansu suka tambaye ta ta dawo gida ne? Ta faɗa musu ta dawo, kuma yanzu ba ta da aure, duk zuwan da suka yi sai ta faɗa musu ba ta da aure, ba ta da miji, yanzu wani auren za ta yi, duk tana hakan ne saboda su kai wa mahaifinsu labari, ko zai tuna da tsohuwar zuma ta fi magani, sai dai sati uku kenan ta ji shiru. Sati na huɗun ne da ya zo ɗaukar su da daddare ta fita da kanta raka su, duk da dare ne amma ta lura da yadda ya ƙara ƙiba, har yanzu yana nan da halinsa na nutsuwa, kamilin namiji, a zuciyarta ta dinga ayyana tabbas ita doluwa ce da ta yarda ta bar shi saboda kucakar ƴar aiki irin Kursum. Suka ƙarasa ta gaishe shi, ya amsa babu yabo babu fallasa, ya haɗa kan yaran za su tafi, ta ce"Sadiq!" Ya juyo ya ce"Yusra akwai wani abu ne?" Ta dake ta ce"Babu komai, amma na yi zaton da ka gan ni na dawo gida za ka tambayi jin ba'asi". Ya ce"To Yusra ai yanzu ba ni da wannan hurumin, ke matar aure ce, gaisuwar ma don dai da yara a tsakani ne, ku wuce mu tafi". Ya faɗa yana kama hannunsu, sarai ya san ba ta da auren, don yaran sun faɗa masa har sau biyu, kuma ya bincika ya ji, shi ma yana ƙaunar Yusra fiye da zato, kawai dai duk wata harka ta ƙasƙanci ba ya cikinta, ita ta nemi rabuwa da shi, saboda haka ya zaɓi a rabun har abada ko da kuwa zai mutu da sonta, indai ba ita ce ta dawo ta canza ra'ayi ba, babu dalilin da zai saka ya sake neman soyayyarta. Har ya wuce ta ce"Sadiq ba ka san auren ya mutu ba har ma na gama idda?" Ya ce"Subhanallah! To Allah Ya yi zaɓin alkhairi". Ta ce"Amin, ina son tattaunawa da kai mai muhimmanci". Ya ce"Ok, idan kin je chamest ki yi mini magana zan shigo". Washegari kuwa tun safe ta shiga chamest saboda shi, bayan ya zo Yusra ta yi ƙoƙarin sauke duk wani jiji da kanta ta bajewa Sadiq sirrint zuciyarta tsaf, sannan ta faɗa masa ta shirya komawa aurensa a karo na biyu. Murmushi kawai ya yi, ya ce"Yusra kenan, irin wannan yanke hukunci haka tamkar ba da umarni? To sai dai ni kuma yanzu mijin mace ɗaya ne, tun ranar da kika ce kin bar sona ba kya kishina ni ma na cire naki na ajiye, saboda haka..." Ta ɗaga masa hannu zuciyarta na bugun fargabar halin da za ta shiga ta ce"Ok, shi kenan na fahimce ka, na gode". Ya yi dariya ya ce"Kar ki yarda hawayen su sakko, Yusra da gaske ashe za ki iya sake yi wa soyayyata kuka a rayuwarki? Na gwada ki ne kawai, na san aurenki ya mutu, amma ban san kin gama idda ba, tun da na sake ki kika gama idda nake cike da fargabar wanda zai aure ki, ina kishinki sosai Yusra, na sake ki ne kawai saboda na faranta miki, tun da hakan kike ganin zai zama mafita a gare ki, ko yanzun kullum cike nake da zulumin wani ya sake aurenki ba ni ba, ke ma har kika nuna kina son mu sake kasancewa a inuwar aure, wane ni da ba zan so haka ba?" Tun da ya fara magana ta sauke ajiyar zuciya, tana kallonsa da sauraronsa sanyi na ratsa zuciyarta har zuwa gangar jikinta, sai ta ji tamar an sauke wani gungumemen dutse daga zuciyarta. Bai bar wurin ba sai da suka gama tsara komai, ta ce masa sadaki kaɗai zai ba ta, sai maganar wurin zama ta ce za su zauna a gidanta wanda ƴan haya suke ciki, kafin ya gama gininsa da ya fara, akan haka suka rabu kowa yana jin zuciyarsa wasai, lallai rabuwa da masoyin asali ba abu ba ne mai sauƙi. Bayan sati huɗu aka ɗaura auren Yusra da Sadiq, ta sake zama matarsa a karo na biyu, sai dai a wannan karon a amarya ta je ba uwargida ba, Kursum ce dai ke da matsayin uwargida kuma yayarta a ala'da, dangi kowa ya yi farinciki da hakan, cikin satin ta sa ya tarkato mata ƴaƴanta, suka dawo, ko hutu ba ta ɗauka ta ci gaba da aikinta, idan tana aiki suna gidan Anti Kursum, wacce ta zo sau ɗaya da tsohon cikinta, ta yi wa Yusra Allah Ya sanya alkairi, ta karɓe ta babu yabo babu fallasa, don a yadda ta tsara sabuwar rayuwarta a gidan Sadiq ɗin, ko da ya gama gininsa sun tare a gida ɗaya da Kursum ko kallo ba za ta ishe ta ba, kowa ya yi harkarsa kawai. Ta so yakicewa ƴaƴanta ƙaunar Kursum ko da ba duka ba, amma da ta ga abun da wuya sai ta rabu da su, kullum sai sun yi mata firarta, a yanzu hankalinta ya kwanta, ta samu nutsuwa sosai take matse kanta wurin hidimtawa Sadiq duk da tana aikinta, don haka suna zaune lafiya ƙalau. Ba ta taɓa zuwa gidan Kursum ba sai da ta haihu, ta haifi ƴarta mace, ta je ta yi mata barka. GIDAN ALI Tun ranar da Hajiya ta yi barazanar za ta kai shi Hizba suka zauna da ƴan'uwansa aka tattauna, suka je gidan Hajiyar, ta kira ƙannanta maza biyu da mace ɗaya, wanda su ne kawai ba su guje ta ba, suka tattauna da iyayen Ali, ta ce ita ba ta buƙatat kuɗinsa, kawai tana so ko yaya ne ya nuna ya san da zaman cikin nan, ko a waya ne ya dinga jin lafiyarta, sannan idan ta haihu yana da zaɓi biyu, ko dai ya aure ta su raini ƴaƴansu, ko kuma ta kawo masa ƴaƴansa ya nema musu mai raino, suka tsaya akan sai ta haihu za a san abun yi. Da lokacin haihuwa ya yi, kwana biyu tana naƙuda a tsaitsaye, ba ta je asibiti ba, don maƙotanta da suka saba da su sun faɗa mata duk a gida suke haihuwa, ranar da haihuwar ta zo gadan-gadan, suka kira mata nurse ɗin da take karɓar haihuwar, tun la'asar har bayan isha'i ba ta haihu ba, ganin ta galabaita sosai ya sa aka tattara aka tafi asibiti, a can ma dai shiru sai wahalar da take ta sha, har Ali da mahaifiyarsa suka ƙaraso, don ƙanin Hajiyar ya sanar musu. Ƙarshe sai tiyata aka shiga da ita, an yi nasarar ciro yaran, namijin babu rai, macen da rai amma ba ta da lafiya saboda galabaita da suka yi, ita kuma Hajiya Allah Ya karɓi abarsa, gabaɗayansu sai da suka girgiza da jin mutuwar ba Ali ba har mahaifiyarsa, ƴan'uwanta suka fara kiraye-kirayen waya ana sanar da mutuwarta, yayinda Ali ya koma gefe ya zauna yana hawayen tsoron Allah da nadama da suke shigarsa a lokaci ɗaya, ya dinga tuna komai na alaƙarsu tun farkon haɗuwarsu ta sanadin Reza, duniya abar banza, Hajiya an tafi tafiya ta har abada, ba don an shirya ba,ba don burika sun ƙare ba, sai don amsa kiran mai sama wajibi ne babu jinkiri. A asibitin ya kwana, sai kashe wayarsa ya yi saboda kar Maryam ta kira ya rasa abin da zai faɗa mata, washegari da safe aka tafi da gawar Hajiya gidan iyayenta, aka sallace ta, ana kai ta ya koma gida, sai ya faɗawa Maryam ƙaninsa ne ba shi da lafiya, suka kwana a asibiti, amma yanzu an sallame shi, ya ce mata zai tafi aiki, ko abinci kasa ci ya yi, ya ce ya sha shayi a gidansu. Wurin ta'aziyyar ya koma, ya tarar har an watse ma babu kowa sai ɗaiɗaikun masu shiga gaisuwa, don an sanar da cewar babu zaman makoki. Jaririyar kwananta biyu a asibiti aka dawo da ita gida, mahaifiyar Hajiya da ta fi kowa ɗaukar zafi da Hajiyar sai ga shi jikinta ya yi sanyi, kamar ma ta fi kowa jin ciwon mutuwar, ta ce ita ce za ta riƙe jaririyar har ƙarshen rayuwarta, to sai dai ita ma ashe ba mai rayuwar ba ce, ranar sadakar ukun Hajiya ita ma ƴar ta bi ta, shikenan Allah dai ya ƙaddara Hajiyar yankakken baya gareta. Da wannan case ɗin Ali ya mutu gabaɗaya, ranar sadakar bakwai da ya koma gidan iyayen Hajiya, mahaifiyarta ta roƙe shi kan don Allah kar ya sake zuwa, don ganinsa yana tuna masa da laifukan Hajiyar kuma ba ta son haka, daga ranar bai sake zuwa ba, ya rufe babin rayuwarsa ta baya, take fuskantar ta gaba. Aliyyu ya tuba, tuba irin wanda yake jin ko da zai rayu babu aure har abada ba zai sake riƙe hannun matar da ba halalinsa ba,rayuwar farinciki suke yi sosai da Maryam, ta haifa masa ɗansa namiji mai kama da shi, yaro har ya yi wayo, amma fa har yanzu halinta na saka masa takunkumi yana nan, sai dai yanzu ta sassauta, idan ya kai dare a waje sai dai kawai ya ga ɓacin rai a fuskarta, kullum cikin gyaran jiki take, yanzu ganin wautarsa ma yake yi yana tunanin da me ya gani a jikin wasu matan, yana da mace kamar Maryam? Don ta sakar masa jiki sosai, ko wanna hadisin nata ta na ba a tashin mace daga bacci ta manta da shi. Allah Ya rufa masa asiri ba ta taɓa sanin zancen cikin shi da marigayiya ba, bai sani ba ko a gaba. Rayuwar Halima kullum ci gaba take samu, ta yi kyau ta zama babbar mace, ta shige cikin ƴan'uwan mijinta suna ta wayar mata da kai akan abubuwa da dama na rayuwa, ta haihu lafiya ɗanta namiji, bai isa yaye ba ma aka yaye shi surukarta ta karɓe shi, saboda wani cikin da ta samu. Zaman su da Anti Aisha har yanzu babu wani canji, sai dai sam ba ta nuna baƙinciki kan ɗan Halima, tana jin son yaron sosai, duk da tana kishi a ƙasan zuciyarta, yadda idon mijinta ya rufe akan soyayyar yaron da sabon cikin jikin Halima, amma tana ƙoƙarin dannewa, tun da sam shi da Halima babu wanda ya taɓa yi mata fariya ko wani abu mai kama da gori akan yaron. Ta manta da babin rayuwar gidan Haruna, duk da dai ta ji labarin aurensu da Zainab. Mutanen unguwa har sun fahimci yawon ta zubar da Zainab take yi, shi kuwa Haruna ya mai da hankali a kasuwa, don samo mata abin da za ta ci, da sauran hidimarta, bai san wainar da take toyawa ba tsawon lokaci, sai biyu tana samun ciki tana zubarwa, wanda ba ta ma dan ainahin na wane ne ba, na Harunan ne ko na wasu a waje? Shi yasa ma kawai ta yi planing don samawa kanta sauƙi. ALHAMDULILLAH! A nan labarin Wani Auren ya zo ƙarshe, Allah Ya ba mu ikon amfani da darasin dake ciki, idan kun ga kuskure arashi ne, ina neman afuwa,kuma ƙofar gyara a buɗe take. Godiya ta musamman gareku masoyan littafaina,musamman waɗanda suka siya. Sai mun haɗu a sabon labari idan mai duka Ya so. 08028966015