💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *FREE PAGE 1* _______________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki _____________________________ _Bismillahir rahmanir raheem_ *_Shimfida_* _Lu'ulu lu'ulunne dai ya yardar Allah,shimfidaddiya kuma miqaqqiyar tafiya dake dauke da wani sabon zubin labari_ _manyan qasashe guda biyu da taurarinmu zasu kasance mallakin qasashenne,wasu abubuwa da guraren zasu iya sabawa da yadda ainihin zubi tsari da kuma yanayin da qasar ke rayuwa akai_ _fatan shine cimma gaci.......fatan shine cimma anihin saqon da alqalamin HUGUMA ya sauka a kai_ _wani sabon salon labarine dake dauke da sarqaqiya.......boyayyun qulle qulle da ZARGE wanda bahaushe kewa kirari da mugun qulli_ _sarauta QASAITA DA IZZA ne zallarta take magana cikin wani irin salo me ban qayatarwa_ _karki bari.......karki sake......kada kuma ki yarda a baki labarin tafiyar nan ya kasance ba dake aka yita ba_ _Allah ya bamu sa'a,yadda muka fara yasa mu kammala a tare cikin qoshin lafiya arziqi da kuma wadata_ *AGADEZ* *masarautar agadez* *_Maison de i'emir_* Masarutar agadez,babbar masarauta ce data kafu tsahon shekaru masu yawa. Ta samo asalin kafuwarta tun daga wani qarni can baya daya wuce,wanda aka samu rarrabuwar kawuna gurin masu buqatar mulkar yankin daga kowanne gida iyali da kuma dangi. Rashin samun hadin kan fidda mutum daya yayi sanadin yanke hukuncin tafiya zuwa ga daular musulunci ta istanbul,mahukuntan yankin agadez kuma suka nemi agaji wajen basu wanda zai zama shike mulki da yankin,wannan shine ya haifar da samuwar sarki na farko dan asalin daular turkiyya istanbul *MUHAMMAD AGGA_ABBA BIN MUHAMMAD ALMUBARAK*. Sosai auratayya hulda na kasuwanci da cinikayya sukaci gaba da wanzuwa tsakanin qasashen nan guda biyu,wanda ta haifar da haihuwar mutanen da suka kasance *RUWA BIYU*. Wato halfcast inji bature. *BUZAYE* na daya daga cikin qabilun da suke da yawa sosai cikin qasar agadez,wasu irin launin mutane dake da wani kyau na musamman daya zame musu tambari na daban,ya kuma sanya suka zama na musamman. A cikinsun SULTANE MUHAMMAD HAMUD ya fito. Mahaifinsa buzu ne na asali,wanda jininsu ya gauraya da na turkawa,don kuwa mahaifiyar SULTANE MUHAMMAD HAMUD 'yar asalin garin istanbul ce......wannan ya sanya kyanshi ya zama wani irin nau'i na daban daya gadoshi daga bangare biyu wato UWA da UBA. SULTANE MUHAMMAD HAMUD......qasaitaccen sarkin da yake mulkin qasar agadez a yanzu. Wata irin hamshaqiyar sarauta dake cike da izza qarfin mulki dana iko gaba daya. Sarkin da yasha banban da dukka sarakunan da sukayi mulkin kafin shi......sarkin daya kawo gagarumin sauyi ya canza qasar agadez gaba daya daga fuska yanayi da tsarin da take a baya,zuwa wata sabuwar duniya datasha banban da kowanne yake na qasar NIGER gaba daya. AGADEZ din a yanzu ta zama wani yanki ko kuma gunduma ta musamman.......yankin daya fadada ta fuskar noma kasuwanci ilimi da sauransu. Wannan sauyin bai tsaya a iya yankin AGADEZ kawai ba......yayi mamaya har ya zuwa cikin ainihin gidan sarautar yankin. Komai ya canza daga inda yake zuwa wani bigire dake tafiya da zamani.....wani yanayi dake dauke da kowanne ci gaba na zamani,ya zamanantar da komai din da wani irin salo da dole kowa ya sallama. Cikin qauna ga sultane muhammad hamud da girmama duk wani motsi da aiki nasa suka bashi sunan ZAMANI GOMA. Qasaitaccen sarki,ma'abocin izzar dake barazana tare da kad'a zukatan abokan burminsa.......qasaitaccen sarkin da kwarjinsa ya keta ta cikin kowanne hijabin BARAZANA......qasaitar data dasa shakka tsoro da kuma kokwanto akan zuciyar duk wani dake da zaton yakai ya tsaya gurbi guda dashi......kwarjinin daya zama wanzajjen abu dake ea matuqar tasiri,ya kuma sanya zukata da yawa sallamawa....... Yana da wani irinn qualities yana da wata irin ZARRA yana da wata irin jajircewa.......saidai duk da hakan akwai wani RAUNINSA guda daya.......RAUNI ne da ba zai taba canzuwa ba.......bazai kuma taba shafewa cikin rubutacciyar qaddararsa ba. RUHINSA ce ita......wani bangare ce ta RAYUWARSA.......GUDAR TSOKA daga zuciya da kuma jikinsa.......ita din wani abune me muhimmanci da ta zama shaida ga kowa cewar.......ba wani abu me tsananin muhimmanci da idanu ke iya ganin ya MALLAKA kamar ita. *_khadeeja(AKHNAN)_* *_Duk kuwa da tarin baiwar dake lullube da rayuwarsa......amma yana jin kamar daban TAKE cikin komai nasa. Tarin dukiya madararta,izzarsa......mulki da DAUKAKAR suna data mulkinsa wadda ta gangara cikin kowanne lungu da saqo na qasarsa.....qasashen africa GABA DAYA dama wasu daga cikin qasashen qetare_* *EMIRE PALACE* _Palais de i'emir_ Wani bafaransen gine ne ko kuma mu kirata DUNIYA ta musamman dake zaman kanta tsakiyar bagargajiyen ginin masarautar AGADEZ din. Gini ne da dake tsakiyar manyan katangun masarautar agadez dake qara nuna qarfin iko dana izzar da masarautar ke dashi. Zaka tadda gine gine iri daban daban dake nuna gargajiya da kuma ainihin al'adar gidan sarautar dake bisa tsari da kuma zamani......zamanin da bai sanya alamu ko burbushin gargajiyar bacewa ba saidai ya gyarata daga ainihin asalin GARGAJIYAR zuwa GARGAJIYARZAMANI. Wani taswira ce da aka tsamota kacokam daga qasar France,qasar da a baya ta zama uwa kuma uwar goyo ga qasar ta nijer,aka kawoshi aka ajiye cikin gidan sarautar sultane muhammd hamud. Katafaren VILLA ce wadda ita ke zama mafaka kuma mazauni ga iyalan SULTANE MUHAMMAD HAMUD. Duk kuwa da cewa matanshi na auren biyu ne........amma kuma villa din na dauke da sassa guda shida ne. Sassa uku dake cikin villa din tafi kowanne sassa na ginin girma kyau fadi tsaho da kuma tsaruwa,biyu na matansa ne daya mallakin me alfarma sultane muhammad hamud,sauran an ajiyesu ne saboda baqi da kuma hadimai. Duk sashe daya yakai girman wani mansion House na mutum guda,wannan ya sanya akwai tazara sosai tsakanin wane da wane,kuma kowa yake rayuwarsa ba tare da damuwa ko takura daga dan uwansa ba. Bata baki ne kawai a gareka a wannan rana ta juma'a tsaiwa tambayar wani "Akwai wani gagarumin taro ne da zai gudana?" Domin kuwa tun daga gate din farko da zai fara kawowa farfajiyar farko da zata kaika farfajiya ta biyu wadda zata sadaka da villa din mai alfarma sultane idanunka zasu iya ganin komai. Yawaitar zirga zirgar hadimai maza da mata.........canje canje da sauye sauyen da akewa wash flowers da sauran kayan alatun da suka zama cikar ado da qawar villa din,duk kuwa da cewa wannan din ba baqon abu bane,kusan koda yaushe wannan villa din cikin tsari take da kuma gyara bisa kulawar manyan jakadun guda biyu da villa din ke dasu *AYAANA* da kuma *ME WADA*. A qarqashin ayaana da me wada kuwa tarin bayi ne.......dogarai da kuma ma'aikatan da kowanne yake jagoranci da rarrabuwa ayyuka iri daban daban,wadanda sune suke tafi da kowacce rana da wuni na villa din. Iyakar nan dinne kawai tasu iyakar da hurumin,kaman yadda kowanne dogari da bawa yake da nashi iyakar da hurumin cikin gidan. Duk da yawan canzawar motsi da kai kawo dake wanzuwa a villa din harma da gidan gaba daya,hakan bazai hanaka ganin daga bangaren da wannan motsin yafi yawa ba. Sashe ne da yake mallakin hajiya *ZAITUN* uwar gidan me alfarma sultane hummad hummad wanda ke amsa sunan *UWA* ga *AKHNAN*. Duk kuwa cewa ba itace matar farko ga sultane muhammd hummad ba.......amma a yanzun sunan uwar gidan ya zama shine TAMBARINTA........uwa ce ga AKHNAN amma akwai wani dalili daya hanata amsa sunan MAHAIFIYA. Dukka wadannan dalilai hakan bai samu qarfin iko dana dantsen togacewa ko rabata da wadannan *LAQABI* guda biyu ba da take matuqar ji dasu.....fiye da yadda uwa ke ji da jaririnta sabuwar haihuwa UWARGIDAN SULTANE kuma UWAR AKHNAN. Wani qasaitaccen gine ne dake qunshe da dukkan wani kaya na qasaita da kuma alfarma,wanda iya su kadai sun isa gaya maka lallai QASAITA da kuma MULKI ne suke magana. Zaka wuce faluka bayan faluka,gurabe masu yawa kafin ka samu isa bangare ZUCIYAR MASARAUTAR kuma SHALELEN SULTANE take. Wani irin ni'imtaccen parlor ne dake da wani irin girma da kuma tsari......irin tsarin da yake zamewa abun kallo a idanun mutane masu yawa,saboda ba tsari ne da aka saba ganinsa ko ina ba......ba kuma tsari bane da aka saba ganinsa koda yaushe ba. Komai na parlor din ya kasance ruby red color and gold,tun daga kan lafiyayyun curtain na kamfanin NICETOWN dan qasar France,har zuwa Italian royal chairs da parlor din ya laqume har set biyu. Lausasan carpet dake nuna zallar alfarma da qasaitar falon dama dukkan abinda ya mallaka dake cikinsa......wasu irin qananun side tables mulmulallu dake daukan idanu wanda suke mahadi da Italian royal chairs din dake parlor din. Gypsum ceiling ne lullube saman parlor din,wanda aka qawata da wasu kyawawan fitilu da kuma crystal Chandelier daga tsakiyarsa. Iya su kadai abun kallo ne da zai daukeka shudewar wasu daqiqu kana mamakin yadda aka baje fasahar samar da ceiling na musamman irin wannan. Akwai qofofi kusan guda uku dake tattare da parlor din. Saidai qofa mafi daukan hankali itace qofar qarshe dake qunshe da wani kyakkyawan corridor maras zurfi da fadi sosai,saidai an qawatashi da wasu irin artwork frame da aka maqale a kowanne bango na corridor din a qalla frames shida. Kowanne frame yana dauke da zane mai daukan hankali na wasu irin furanni da qananun tsuntsaye a kansu,iyakar abinda yake jikin frame din kenan. Qofofi uku ne,abinda yake baka daman gane cewa bedrooms uku corridor din ya mallaka,kuma kowacce a qofa a rufw take ruf,sai guda daya da bata kai ga rufewa gaba daya ba. *PRINCESES* kamar yadda yake a rubuce a saman qofar dakin.....qofar dakin da idan ka samu nasarar budeta zai baka daman cin karo da wata ALJANNAR DUNIYA ta musamman. Komai na dakin na musamman ne da wani irin tsari da kalolin da kana ganinsu kasan cewa zabi ne na mamallakiyar dakin. Mutum shida ne cikin bedroom din masu mabanbantan yanayi kamanni dama matsayi na rayuwa. Zagayayyen gadon me suffar oval shape wanda yake lullube da rumfar net ta alfarma idanunka zai fara sauka. Kyakkyawar matashiya ce zaune a samansa......matashiyar da duka shekarunta ba zasu haura ashirin da hudu ba. Fara ce tas......irin hasken nan me fita sosai,ma'abociyar yalwar suma data bayyana harta qasan dankwalin lallausan material din dake jikinta. Tana kyan da a kallo daya zaka yarda da hakan,bata da jiki sam,siririya ce da rashin qibarta ya bayyana ta cikin lallausar doguwar rigar jikinta. Daga gefan gadon take a zaune amma qafafunta suna zube a qasa,gefan damanta kadan wani kyakkyawan table ne dake dauke da madaidaicin tray da aka shirya apple a ciki da grapes da basu da yawa sosai masu bala'in kyau........wanda sukan kasance zababbu cikin kayan marmarin da dukka za'a tsinko kuma a shigo dasu zuwa sassan AKHNAN. Qafarta daya saman daya,yayin da idanunta suke kan wata matashiyar dake tsaye dan nesa kadan da ita da alama magana take da ita me muhimmanci. Matashiyar da suka sha banban da wadda ke zaunen da wani nisan tazara me tarin yawa......wata irin tazara da babu shakka za'a jima ana ragaita cin neman halittar da zatayi tsara da ita. Bawai magana ake ta MATSANANCIN KYAU ZALLA BA.....aah...wani irin kwarjantaccen yanayi ne madararsa ke lullube saman zagayayyar fuskar da Allah ya horewa wani irin kwantaccen kyau daya cakuda daga mabanbantan qabilu guda biyu. BUZUWA CE ta wani fannin kuma jinin qabilar TURKAWA CE tsatson Istanbul. Wasu irin kyawawan idanu Allah yayi mata baiwa dasu,masu dauke da wani kebantaccen yanayi na kwarjini da wani irin kyau da ba zaka iya dauka idanun dan adam ya kebanta da irin wannan kyan ba. Idanun dake da girma da wani irin shape da ya sanyasu sukan lumshe karan kansu,lumshewar da yake dan rage girman da yake dashi. Matasan 'yammata ne guda daura da inda take tsayen,wanda dukkaninsu sanye suke cikin shigar wani olive green color din yadi,saman kansu kuma hijab ne Vshape apple green daya dace sosai da olive green din jikinsu. A shekarunsu dukkaninsu sa'annin juna ne......kowacce cikin tsafta nutsuwa da kuma tsari take,hakanan akwai alamun nutsuwa sosai saman fuskar kowaccensu. Kusan dukka su hudun kowacce aikin gabanta takeyi. Guda biyu ne bayanta,ta farkon qoqarin zuge zip din gown din dake jikin AKHNAN takeyi cikin matuqar girmamawa da takatsantsan. Gown din da aka dinka da wani lallausan yadi da a kallo daya kawai zaka fahimci sutura ce ta alfarma......sutura ce kuma ta diyoyin isassu da kuma wadanda suka isa. Gown din ta zauna a jikinta tamkar don ita kadai aka halicci yadin,ta kuma sauka har saman dogayen yatsun qafafunta ta lullubesu. Zamanta a jikinta sam bai sanya halittarta fita ba,saboda abune sananne ga duk wanda yake da jibi da sanya suturarta,tun daga me dinkawa zuwa me sauyasu da kuma tsara closet dinta batason matsatsen tufafi sam. Duk da cewa abun a baya yana daya daga cikin tsarukan MAMMINA da wasu ke kira da GIWA a kebantattun lokuta.......amma ta wannan fuskar sai suka sha banban da AKHNAN........Banbanci qwaya guda tallin tal da har yanzu ba wani abu na biyu daya zama sabanin ra'ayi a tsakaninsu. Matashiya ta biyun kuwa tana kusa da waccanne,hannunta dauke da wani babban tray me ruwan gold dake lullube da wani tattausan yanki fari qal,wanda a cikinsa babu komai face kalolin ribbons da hair clip,ta tallafewa matashiya ta uku dake bangaren kafadar daman AKHNAN din tana tufke doguwar sumarta tare da qoqarin lanqwasata gami da qawatata da ado na ribbons masu zallar kyau da tsari. Matashiya ta hudu na daga gabanta a tsaye tana zuba warwaren dake qyalli a santala santalan hannuwan akhnan,wanda ta miqa mata su,idanunta dake dauke qwayar ido kalar baby blue zube saman fuskar matashiyar dake zaune gefan gadon. Har yanzu tana riqe da apple din data gutsira sau daya bata kuma sake ba,still tana duban akhnan,kafin a nutse ta maida apple din tana sauke qafafunta data dora daya saman daya ga gyara zamanta tana cewa "Il lui a vraiment fait du mal(yayi matuqar cutar da ita),har yanzun ta kasa mantawa........ta kasa manta yadda relation dinsu ya taba gudana a baya". Matashiyar ta qarasa fada muryarta tana yin qasa,alamun dake nuna kowacce magana ma sukeyi tana da girma a zuciya dama harshenta. Janye manyan idanunta akhnan tayi tana rufe blue eyes dinta,sannan ta dauke dubanta kacokam daga fuskar matashiyar tana maidawa ga bagaren hannun damanta,ta sake zube lumsassun manyan idanunta saman window size mirror din da da hadimarta data gama gyara mata gashinta ta dauko ta ajiyeshi dirshan a gabanta. A nutse ta sauke kallonta tana duban kanta,tun daga qafafunta da gown din ta lullube har zuwa sumarta me yawa tsaho baqi da kuma sulbi. Dakin ya dauki shuru,ta tsaida idanunta saman fuskarta. Kamar kowanne lokaci irin wannan......kamar kowanne zamanin me kama da wannan da yakanzo ya kuma wuce cikin rayuwarta. Ko daya......ko kusa kuma ko alama bata jin kowanne feelings game da lokacin......bata jin wani abune na musamman,hakanan bata jin cewa wani kebantaccen abune daya kamata ta jishi har cikin zuciyarta. "Birra" Ta kira sunanta da tattausan sautin nan nata da koda cikin fushi......koda cikin fada yake fita,wani irin sauti da baya buqatar hayaniya ko wahala. ___________________ zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *FREE PAGE 2* ____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ "Ranki shi dade" Birra din ta matso da hanzari tana sunkuyar da kanta cikin matuqar girmamawa. Da hannu kawai tayi mata nuna data cire duk wani adon gashi datayi mata,sannan ta sauke yatsanta tana cewa "Ruban(ribbon) daya C'est suffisant(ya wadatar)". "Angama" Ta fada cikin son cika umarninta. A gaggace ta matso ta soma zaresu,sannan ta waiwaya gefan da 'yar uwarta take tsaye. "Matso gaba bushira......ki jerasu yadda suke a maidasu muhallinsu" Taku biyu ta qaraso wajen,ta miqa tray din birra na ciresu yana saka mata a kai. Duk da cewa cikin matuqar takatsantsan birra ke cire ribbons din amma hakan bai hanata jin wani abu cikin sumartata ba,ta daga dogayen yatsun ta a hankali tana dafe goshinta cikin salon dake nuna tsantsar gata da rashin sabo da duk wata wahala "Pourquoi?(why)?" Ta furta a hankali tana lumshe idanunta. Tako ina tana jinta a takure,tana kuma jinta a daure,don ita sam bataga dalilin wannan gagarumar takurawar ba.......gagarumin shirin da sam sam take ganin wanda akewa bai cancanci hakan ba......hasalima tana kallon hakan a abinda sam bai dace da ra'ayinta da zabinta ba.......ita akhnan......bata jin akwai wata halitta a nan kusa da takai tsada da darajarta. "Me yasa mammina ta damu haka?,me yasa mammina bata gajiya da yin shiri akan irin wannan wasan kwaikwayon ne AISA?". ta qarashe maganan daidai sanda buhaina ta kammala sarqafe rigar tsaf a jikinta ta kuma ja baya cikin girmamawa ba tare da tace komai ba don kada ta katse maganar da sukeyi ita da aisa din,don ta tabbatar zata ji alamun ta kammala din. Inibin da aisa ta miqa hannu da zummar daukowa ta fasa dauka,ta zubawa akhnan idanu na wasy daqiqu kafin ta waro idanu tana dubanta. "Akhnan?......wasan kwaikwayo kikace fa?,wasan kwaikwayo?........zuwan altaab nu'uman dinne wasan kwaikwayon?". Itama zubawa aisa idanu tayi na sakanni sannan ta furzar da iska daga bakinta tana yiwa bushira,buhaina,birra da barra'u alamun su fita. Ajiye abinda yake hannuwansu dukkansu sukayi,duk kuwa da cewa basu qarasa shiryata kaman yadda mammina ta bada umarni ba......basu qarasa aikin da mammina ta basu babban gargadin su yishi yadda ya dace ba qasa da mintuna sittin kacal......saidai dukkaninsu sun sani.....umarni da maganar akhnan tana iya shafe ta mammina koda ta mammina dince daidai. "Bansan da wanne idanu kike hange ba.....ban kuma san d wacce zuciya kike tunani ba akhnan......maganar shahinaz na gama yi miki yanzun.......saidai bakicemin komai akai ba amma kina neman sake birkita min tunani da maganganunki". Cikin wani irin takunta na halitta tamkar macen dawisu ta qarasa zuwa ga wata Turkish sofa dake ajiye daura da ita ta zauna. Qafarta ta dora daya saman daya,sannan ta aza dukka hannuwanta guda biyu saman gwiwarta,ta kuma ware lumsassun blue eyes dinta ta zubesu saman fuskar aisa. "Shahinaz.......bata da hankali aisa". Akhnan ta fadi karon farko......a karon farkon da tunda aisa ke bata labarin matsalar bata taba tofa komai a ciki ba koda kuwa da wasa ne. Idanu aisa ta fidda cike da kalar wani irin mamaki. " Akhnan?.......kin manta wace shahinaz?.....kin manta yadda yamaan yake a wajenta?". Kamar me nazartar aisa haka take kallonta,kafin ta zuqi wani qasaitaccen numfashi ta fiddashi a nutse ta tsakanin kyawawan labbanta da suka sake qawatuwa da kalar jambaki red mara damuwar haske me yawa. "Ita ta zabawa kanta haka.......ita ta zabi rayuwa tazo mata a haka" Ta fada a taqaice da kalaman da suka sake jefa mamaki saman fuskar aisa. Eh tana mamaki ne badon batasan wacece akhnan ba.......fitar kalaman daga bakin akhnan ba wani abu bane da zai sanyaka tsananta mamaki ba......aah......kawai ta dauka hukuncinta zai iya tsallake case din shahinaz da yamaan. "Duk macen da d'a namiji ke wahalarwa ita taso........darajar diya mace ta zarce ta komai......musamman diya macen da tasan wacece ita,sannan kuma tasan kanta". Tayi maganar tana qarasawa gaban babban dressing mirror dinta da aka yiwa corner ta musamman cikin dakin,ta kuma dauki tissue dake cikin wani royal tissue box ta soma dauke jambakin dake saman labbanta. "Ba zaki gane komai ba akhnan........na yarda,kinyi nisan da bazakiji kira ba........amma idan kika jarabtu da soyayyar altaab nu'umam zaki fahimci komai,basai na bata bakina da nufin yi miki bayani ba". Dif akhnan tayi,saidai hakan bai hanata goge labbanta da tissue din ba,kafin kuma murmushi ya subuce mata cikin qasa da second biyar. Wani irin lallausan qasaitaccen murmushi,wanda ba komai cikinsa sai wannan izzar dake yawo a jininta. Aisa na ankare da murmushi da ya sanyata nazartar akhnan a dabarance,tanason sanin meye ya sanyata murmushin?,don ba komai ke sakata murmushi haka ba. "Altaab nu'umam?.......na yarda qawancanmu tun na quruciya bai gama gaya miki wacece khadeeja muhammad hummad ba.........aisa........banajin a DUNIYA akwai halitta d'a namijin data dace da KHADEEJA MUHAMMAD HUMMAD......har kuma a nade qasa bana tunanin za'a haifeshi,don har yanzun banji qamshi qamshin irin MIJIN BURI na da MAFARKINA BA.........saboda haka bani da tabbacin yin aure NAN KUSA ko a nesa" Takai qarshen maganar tana zuge zip din rigar don sam bata jin ta dace da yanayin da take jin kanta a ciki. Idanu warwaje aisa ke kallonta,ta jima da sanin wacece akhnan........don batajin zata kasance ta biyar ko ta hudu ma cikin wadanda sukayi mata farin sanayya muddin bata tsaya ata uku ba......amma a yau din akhnan ta qarasa wanke mata kanta gaba daya.......ta sake samun tabbaci daga wasu daga kalaman shahinaz aduk sanda hirar akhnan ta taso a tsakaninsu. "Har yau bakisan wacece ita ba......a kullum sabbin halayenta ne suke fitowa......saita rikide mata ta zame maka tamkat hawainiya a wadansu lokutan" "Akhnan........" Ta kira sunanta a birkice tana dubanta,saidai kafin ta qarasa ta waiwayo ta zube mata manyan blue eyes dinta.....kafin kuma kowa a tsakaninsu yace wani abu an taba hannun qofar an turota kadan ta bude. Macace wadda shekarunta na haihuwa suka fara turawa zuwa matakin girma da kadan......shekarun da duka basu wuce a sanyasu tsakanin arba'in da biyar zuwa da takwas ba. Sanye take da wasu kayan da suke kama da suturar fulanin nigeria......saidai kuma akwai bambancin ado da kuma launin tufafin. Kanta lullube da wani babban zanin daya kasance nau'in tufafin jikinta,bawai kuma ta lullube kanta kawai bane aah....daurashi tayi saman kanta,girman zanin ya sanya daurin shima yayi girma sosai saman kanta,sai jelar kitsonta masu kauri sosai da suka biyo ta gefen kunnuwanta guda biyu. Labbanta baqiqqirin suke,har sai kayi zaton tana ta'ammali da taba sigari,saidai ko kusa bata da alaqa da wannan,saidai yanayin nata labban kenan wanda yake da tasiri a qabilarsu. Akwai wasu irin zane zane a fuskarta wanda hakan bai hana fitowar kamanninta ba. Tafisu kenan......babbar hadimar hajiya hajja zaitun wato mammina. "Allah shi ruhwa miki asiri.......uwargida giwa ke magana.......tace a gaya miki......dan gidan alhaji nu'uman na dab da shigowa masarauta......ki gaggauta qarasa shiryawa.......sannan ki fara biyawa ta wajenta tana son ganinki". Kyawawan idanunta masu zubin almond ta juya,sannan ta sauke wani sassanyan numfashi sannan ta gyada kanta a hankali kamar batason yin hakan,abinda ya bawa tafisu daman sakin qofar ta jata ta kulleta yadda take. A nutse ta juya sannan ta fara takawa zuwa ga wata qawatacciyar qofa dake manne da dakin baccin,qofar da kai tsaye zata sadaka da wani mahaukacin dressing room dake shaqe da suturu na alfarma. "Kiyi qoqari ki faranta ran sultane akhnan". Aisa dake zaune ta furta muryarta can qasa. Tsawa akhnan din tayi cak,kafin ta waiwayo a hankali,ta zube dubanta akan fuskar aisa din. Sosai taja fasali,kaman zatayi magana amma kuma sai taji babu buqatar hakan,ta dauke kanta taci gaba da takawa zuwa ciki. Kaf kayan jikinta ta fiddasu ta zubesu a gurin,ta miqa hannu ta jawo daya daga cikin lausasan towels dake maqale a sashe guda na gurin ta daura,sannan ta matsa zuwa sashen dogayen rigunanta. Mutum ce da ita da zabinta yasha banban dana kowa......mutum ce da ba lallai abinda yayi maka ya burgeka ko yayi daidai da tsarinka itama yayi mata ba......wata irin mutum ce da zabinta ya zama na daban kuma na musamman......tasan da hakan,tasan kuma dabi'unta fiye da yadda kowa zai gaya mata,wannan ya sanya take da wasu halaye guda uku. MISKILANCI daya gauraya da jinin sarauta dake kewaya duk wata jijiya ta jikinta yakai jinin zuwa ga zuciyarta. DAMUWA DA ABINDA YA SHAFETA ba tare da shiga shirgin kowa ba. Tana iya shafe kwanaki masu tsaho ba tare data bar kowa ya ganta ba......tana iya daukan dogon zamani tana rayuwarta ita kadai. SHAHINAZ da AISA mutum biyu rak da suke cikin rayuwarta tsahon lokaci,tun zamanin quruciya kawo yanzu......mutum biyun da har yau bata canzasu da wasu ba. Ba zasu canzu din bama Sam,don su daya ne suke iya fahimtarta a sanda tayi magana da kuma kafin ta yita,su daya ne takejin zata iya jinginasu da rayuwarta. Ta dauki rayuwarta da matuqar muhimmanci. Ta daki rayuwarta a matsayin SIRRINTA ta dauki rayuwarta a matsayin wani rufaffen abu da bai shafi kowa ba.....bai kuma kamata kowa ya sani ko ya shiga ciki ba. SULTANE da MAMMINA su daya ta yarjewa suyi zartarwa akan lamuran da suka shafi rayuwarta.....duk kuwa da cewa akwai MOMMA a gefe......wanda a idanu da kuma mizanin dacewa ita yafi cancanta da matsayin data bawa mammina.......saidai har cikin jijiyoyin dake tayata rayuwa tana jin matsayin MAMMINA ya shallake na kowa a gurinta......koda kuwa sultane kansa......wani lokaci tana jin sai ya jira MAMMINA. *_uhmmm......tofa_*😟 Moroccan abaya black masu adon Golden din zare da wasu duwatsu masu qyalli ta yiwa kanta zabi. Wata irin riga ce daga sama dake da fadi yayin data cikin ta kasance daidai jikinta. Hade take da wata irin hula da take a mazaunin mayafi wanda ke maqale daga kafadar rigar daya bada yanayi na alkyabba,saidai tako ina tasha banban da alkyabbar,ta darata kyau daukan ido da kuma daraja gurin tsada. Duk da yadda ta saba da shiryata akeyi ta hanyar fidda mata kayan da zata saka,tayata daurewa da miqa mata takalmanta,bata turare powder da sauran kayan qyale qyale amma a yanzun duka taji bata buqatar wannan,ta matsa gaban madubi tana duban fuskarta. Ta maida idanunta ta lumshe a hankali sannan ta budesu tana sake kallon fuskarta. Batasan dalilin da zai sanya sultane da mammina su dameta har haka ba,batasan me yasa suke damuwa tayi aure ba......batasan me yasa suka gaza fahimtarta ba......sun kasa gane cewa babu wani d'a namiji da zaiyi daidai da ita......ba wani d'a namiji da zaiyi daidai da muradinta......ba wani kalan namiji a duniya da zai cika dukka sharuddanta da kuma mizanin da takeso miji a gareta yakai ko ya cikashi. Bata ji a jiki da zuciyarta tana da buqatar aure.........bata kuma buqatar komai cikin rayuwarta.....rayuwarta ta dace da ita......komai yayi mata daidai yadda takeso......komai yana tafiya bisa sonta tsarinta da kuma muradinta......mene MA'NAR AURE a rayuwa irin tata?. "Aure shine cikar mutunci kima da martabar kowacce d'iya mace......koda wacece ita.....kome ta mallaka......ko waye UBANTA!" Kalaman qarshe suka dawo mata daga bakin momma.......kalaman data gaya mata su a ranar data taqi karbar tayin auren Aaroon......tace shima baiyi mata ba kamar sauran mazan. Idanunta ta sake lumshewa ta kuma budesu,wani zafin matar yana dawo mata sabo daga can qasar zuciyarta. A duniya ita daya ce tak take iya gaya mata duk maganar da taso........ita kadai ce take gaya mata duk maganar data fito daga bakinta.......bayan mammina da sultane.....ita daya qwallin qwal take saka idanunta cikin nata ta gaya mata abinda dukka taso. Har yanzu zuciyarta taqi gamsuwa da matsayin matar a wajenta.......har yanzu taqi karbar wannan matsayin nata da wai sultane yake gaya mata ako da yaushe a kanta,zuciyarta ta gaza aminta da hakan harta kalleta da wannan matsayin. Ko waye......ko kuma su waye zasu bata mata rai....komai girma matsayi ko shekarun mutum indai a kanta ne sai inda qarfin mammina ya qare.......amma ta rasa ME YASA ta kasa takawa matar burki a kanta?,ta rasa wacce irin kara sultane yake mata a kanta?,batasan me yasa suka barta ita da ita ba har take yawan shige mata hanci da qudundune?. Ta fiya fada.......tana da zafin da bata ganin wanzuwarsa akan kowa sai a KANTA ita daya......ita akhnan. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *FREE PAGE 03* ______________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ______________________________ A karo na uku ta lumshe idanunta sosai har kaman ba zata budesu ba,yayin da kunnuwanta suka shiga dauko mata wani baqon sauti da wata baquwar busar data tabbatar bata masarautar agadez bace. "Yanzun kam kya fito haka.....don na tabbatar kinji isowar baqinki" Aisa ta fada wadda ta tsaya gaban console din dake dab da dakin tana gyara daurin dankwalinta,wani irin dauri na musamman da aka sarqafashi da nau'in yadi guda biyu. Sai data sake bata wasu mintuna tana rarrashin kanta kafin ta juya ta saka hannu ta jawo wani plate shoe me azabar kyau da aka yiwa ado da gashin jimina,abinda ya qara tsadar takalmin da kuma darajarsa kenan,ya kuma sake fidda ainihin izza da sarautar dake tattare da ita. Baki kawai aisa ta sake tana kallonta sanda take fitowa,amma sai akhnan din tayi kamar bata ganta ba,ta soma takawa cikin takuntan nan da ya banbamta ainun dana sauran mata. Wata irin tafiya da duk sanda aka zauna hirar mata cikin masarautar sai sun tatauna akai,duk kuwa da cewa ba kowa yayi katarin taba ganinta ba. Akhnan din wata kadara ce me tsananin tsada cikin masarautar,kalar kadarar da ganinta yake zama wata babbar sa'a ga duk wanda ya samu dama ganin nata. Sarauta ba qarya bace,kuma da gasken tabi jinin akhnan din da kyau,tun tana zanin goyo bata gama sanin wacece ita ba aka horeta akai.......ta taso a cikin ta,saita zame mata tamkar RAI DA NUMFASHI. "Amma......biftu(sunan da akan kirata dashi Musamnan ga ahalinta na kusa sosai da ita,kamar shahinaz din da aisa),kinsan ma'anar saka baqin kaya da kikayi a al'adarsu altaab nu'umam kuwa?" Aisa ta fada tana tsaiwa cak?. Maganar aisa ko daya bata saka akhnan tsaiwa ba......saima ci gaba da takawa da tayi da irin takun dake gayawa aisa SARAUTAR ta motsa mata. "Kina iya biyoni.....kina kuma iya zama,ban shirya yin komai don farantawa wani d'a namiji daban ba........ban dauki halittarsu wata aba me muhimmanci ba da zanyi komai don na burgesu ba.........kawai darajarsu guda daya ce........da abaat(sultane muhammad hammud)ya fito a cikinsu" Tayi maganar sanda take sanya qafafunta don fita a dakin. Cikin kwarjinita take takawa tana ratsa sassanninta zuwa sassan mammina. Wani kwarjini da kusan gadonshi tayi daga wajen abaat dinta wato sultane muhammad hammud,anyi ittifaqi a tarihin qasar agadez ba'a taba sarkin da yake da kwarjini irinsa ba. Da yawan sukan fadi maganganu akan irin kwarjininsa,wasu sukance nema yayi......wasu kuma suce dabbar daji yake ci wadda take da irin wannan tasirin a jikinta,yayin da wasu ke alaqanta hakan da yawan ibada da yake da ita da riqe dokoki da shari'ar Allah daidai gwargwado,wannan ya sanya wani haske na musamman da kwarjini ya wanzu a fuskarsa. (Tabbas.....ga duk mutumin daya riqi ibada zaka sameshi da wani irin kwarjini.......zaka samu wani haske na musamman akan fuskarsa darajar wannan ibadar,Allah ya bamu dacewa ya sanyamu daga cikinsu ameen). Birra buhaina bushira da barra'u,suna cikin amintattu kuma hadimanta makusanta. Cikin tarin hadiman da take dasu su kadaine mafi kusanci da ita. Zababbun hadimai da aka mallaka mata su,wadanda asali iyayensu da kakanninsu suma amintattu ne ga sarki muhammad hammud dama iyayensa. Wata qarin daraja ce me yawan gaske samun damar zama hidimi ga ZUCIYAR SULTANE wato AKHNAN,wata dama ce da mutane da yawa sukaso ta kasance dasu,saidai su din suka samu saboda aminci da nutsuwa da kuma nagartar halayensu dana mahaifansu. Suke take mata baya cikin kula da kowanne taku nata da kuma inda suturarta dake sharar qasa take sauka. Aisa na gefanta tana amsa wayar da akhnan batasan ta waye ba,don hankalinta ya tafi kan yadda zirga zirga ta ragu a sassan mammina din cikin qanqanin lokaci. Tasan wannan aiki ne da kuma umarnin mammina........ba yau ta fara yin baqi makamantan altaab ba,a duk lokaci irin hakan kuma takan hana yawaitar zirga zirga a cewarta kada a rabawa diyarta hankali,har sai ta gama ganawa dasu sun wuce. "Barka da fitowa ado kuma zinariyar SULTANE" Abinda bakunan da yawa daga cikin hadiman sassan mammina ke fada kenan cikin girmamawa da yin qasa da kawunansu. Su birra ke amsa mata,suna kuma biye da ita,sukaci gaba da wuce faluka har suka kai bakin wata pivot door da akayi mata zubin masarauta sosai. Sakin mata rigar sukayi suka kuma ja baya,don tasu iyakar kenan,saita sanya kai zuwa parlor din bayan ta tura qofar,ita da aisa suka sanya kai. Tana tsaye gaban wani kyakkyawan madubi da zakayi zaton fuskarta take kallo,saidai kuma ba haka bane,qaramin kaskon turaren wutane a hannunta wanda qamshin turaren ya gama zama a parlor din tun wani lokaci me tsaho daya shude. Duk da bata waiwayo ba amma ko a iya haka zaka iya gane tsahon da take dashi. Giant ce wadda ke sanye da wata irin riga da laushinta kawai zai saka ka kasa kiranta da alkyabba. Ba komai a jikin rigar sai wani irin zanen adon dawisu ruwan bula(blue color) da yarfin ruwan dorawa cikin zanen jelarsa. "Assalamu alaikum" Aisa data ajiye kiran da take amsawa tayi sallamar,abinda ya sanya matar amsawa kafin daga bisani ta waiwayo fuskarta fadade da murmushi. Da dan sassarfa akhnan ta soma takawa,ta isa ga matar ta rungumeta sosai gami da shigewa jikinta,sai ka rantse qaramar yarinya ce da duka shekarunta basu haura uku zuwa biyar ba. Da madaukakin murmushin nan ta maida hannuwanta ta lullubeta da kyau,sannan ta jata kujerar kusa dasu ta zauna tana zaunar da ita a gefanta. "Kyau gadon gidanku ne diyata......kinyi kyau matuqar kyau.......amma me yasa su birra suka baki suturar da ba ita na basu ba?" Mammina ta qarasa maganar idanunta akan fuskar aisa. Dukka girarta isa ta dage tana qarasowa ta zauna saman hannun luntsuma luntsuman Royal sofas din dake parlorn. "Duk cikinsu kowa yayi aikinsa yadda ya dace yayi.......matsalar daga gurinta ne,c'est une fille têtue(she's a stubborn girl)" Ta qarasa maganan tana jefawa akhnan harara. Idan tana gaban mammina din komawa take tamkar wata jaririya,wani irin gata da kuma kulawa mamminan take bata,zaka dauka yau aka haifeta tsabar kulawa da riritawa. "Daina fadin haka aisa........shi maraya a kullum abun nuna kulawa ne......abun ayi masa abinda ranshi keso ne,ba'a bari hawayen maraya ya zuba ko a sakashi a damuwa" Ta fada tana dafa kan akhnan. Ire iren maganganun mammina kenan da kullum suke qarawa akhnan qaunarta,duk da tana jin cewa ita bata rasa mahaifiya ba sam sam,tunda gata ga mammina din.......bata taba sanin radadi ko ciwon rashin uwa ba tsahon rayuwarta.......tana jin mammina ta maye mata gurbi,gurbin sama da uwa ma. Sosai ta qanqame mamminan tana sakin qaramin murmushi,tana kuma iya hangen yadda aisa ke jifanta da harara. "Tashi muyi magana akhanan" Mammina ta fada tana gyara muryarta. Sosai ta miqe ta zauna tana zubewa mammina blue eyes dinta da suka rusuna suka rage girma. Itama idanun akhanan din take kalla wani abu yana huda zuciyarta. Idanu ne da kullum ta kallesu saisun taso da wani tsohon birnannen abu daga zuciyarta.......idanu ne da idan ta kallesu kullum sai sun tuna mata da wani abu......wata rana.......wani lokaci dukka da suka shude shekara ashirin da uku a baya. "Altaab nu'uman" Mammina ta fadi sunan daya sanya girar akhnan tsukewa kadan. "Yana da dukkan ingancin da nake zaton ya isa a soshi akhnan,wannan dalilin ya sanya na bashi qofar zuwa gurinki da amincewar me martaba.........ki nutsu akansa da kyau,idan yayi miki shikenan,idan baiyi miki ba babu me tilastaki......wannan din alqawari ne muka yiwa kanmu ni dame martaba". Sai data zare jikinta daga na mammina sannan ta gyada kai. Qasan ranta kawai takeji wannan din bata lokaci ne da kuma bata bakinta kawai da mammina keyi din,gaba daya tsakanin jiya da yau tana jin kamar an bata mata awanninta ne kawai,tasota da sultane yasa akayi tun daga niamy......ya banbareta daga kan aikinta,ya barota daga ayyukan kamfaninta da take tsaye a kai,wani abu guda da bata taba gajiya dashi.......wata hidima qwaya daya da bata taba jin ta qosa da ita ba.......hidimar kamfaninta........kasuwancinta........kuma babbar kadarar da kaf cikin kadarorin sultane Muhammad hammud babu me kima da darajarta........wadda soyayyar da yake mata ya sanyata sallamar da ita ga AKHNAN din. Wannan din wani abu ne da yayi matuqar girgiza zukatan mutane da dama.........abune da ya bada mamaki ainun cikin masarautar gaba daya. Wani abune da ba'a taba hasashen faruwarsa ba tsahon zamanin,domin kamfanin ZUCIYA ce ta dukiyar sultane dama abinda ya mallaka. Faruwar abin ya bude wasu qofofi da dama da a baya suke a rufe.....ya bude wasu qofofin da ba'a taba tsammanin budewarsu ba.......ya kuma qarasa bude wasu da motsi kadan suke jira su bude din. Yabar wasu irin tabbai.....da muhimman al'amura cikin zukatan mutane da yawa.......hakanan ya gadar da wani gagarumin shirin QUDURI da baisan zai zamewa rayuwar AKHNAN din BARAZANA BA......barazanar da take ci gaba da bibiyarta ba tare da idanun masu kallo nazari ko hasashe sunkai kai ba. Da kanta mammina din ke biye da ita a baya tana kuma jeranta mata addu'o'in samun daidaito tsakaninta da altaab nu'uman,addu'ar da akhnan ke ji tana mata yawo akai da zuciya......tanason cewa mammina tabar addu'ar nan haka don bata tunanin zatayi amfani a wannan muhallin da gurbin,saidai miskilancinta dake a kusa ya hanata buda baki tace da mammina komai. "Allah shi ja kwananki.........Allah shi karya maqiyanki". Kakkaurar muryar ta karade parlorn farko da mammina......wanda daga shi sai 'yar farfajiyar da zata fiddaka da sashen. A nutse akhnan ta daga kanta tana ajiye dubanta daga sashen da take jiyo sautin. Tamim ne,mutumin da har yanzu ba zata iya tuna ko tantance lokacin daya samu kansa wanze cikin masarautar ba. Bama ita kadai ba,kusan duk wanda ke cikin masarautar bazaice ga sanda tamim ya zama halalin masarautar ba......ba wani wanda zai iya dorar da komai a kansa........an wayi gari yana rayuwa a masarautar kamar sauran al'ummar masarautar........kamar kuma yadda sauran hadiman cikinta ke rayuwarsu. Yana da wani irin ladabi da ya siya masa kusanci da qauna me tarin yawa daga wajen mammina..........yana da wani irin biyayya da d'a sama da biyayyar bawan da ubangidansa ya zuba kudade masu kauri ya siyeshi........tamim din ya samu wani kusanci da sultane muhammad hammud ta hannun mammina din,wanda ha jima da zama dan gidanta.......kuma amintaccenta da ya kasance lamba na daya a bangaren maza hadimai na gidan. Yadda yake nuna qauna da kulawa ga akhnan........yadda yake nuna sadaukarwarsa akan duk wani sha'ani nata.......yadda yake nuna fansar ransa game da masarautar agadez dama duk wani lamari daya shafeta ya sanya ya sake samun shiga sosai wajen sultane muhammad,ya bashi yabo ya kuma bude masa wata qofa ta aminci yarda da kuma kusanci. Tun kafin ta gama zama KHADEEJA take ganin irin wannan tsananin girmamawa daga tamim. Girmamawar da har qasan ranta duk da tarin izzarta da sarautar dake yawo a jininta takejin tafi qarfin nata girman. Ba zata taba iya tuna wata raba qwaya daya ba tun bayan data mallaki hankalin kanta da tamim ya taba tsaiwa a gabanta alhalin tana tsaye ba bare kuma a zaune,ba zata taba tuna wata rana guda daya da tamim ya hada idanu da ita ba ko ya gaidata yana sanya idanunshi cikin nata ba. Ire iren wadannan abubuwan suka sayawa tamim din wata 'yar daraja kadan daga gareta,duk kuwa da cewa ba zaka taba fahimtarta akan hakan ba koda da motsin yatsan hannunta ba. Abu guda daya ne da har yanzun takeji game dashi,bai kuma taba gusawa ko motsawa daga ranta. Yanayin zubin halittarsa da qirarsa da idan ka kalla zakaga tasha banbam data sauran mazajen qasar agadez......hakanan kuma tayi banbanci da dukka qabilun dake qasar niger gaba daya. Idan kayi masa kallon farko aka ce maka "Wannan din mutumin kirki ne" A karon farko zaka qaryata hakan,don babu wata siffa tashi guda daya dake nuna haka,saidai kuma mu'amalarsa sauqin kansa da kuma irin girman daya runguma yake basu gaba daya zai gaya maka gaskiyar abinda aka gaya maka da farko. Ta gota tamim da taku kusan uku,amma haka kawai taji kamar an fusgi hankalinta. Ta waiwaya kadan ta saci kallon inda yake duqe har a sannan kanshi a qasa,mammina kuma na tsaye a gabansa ta dakata daga tattakin da take musu. "Wanne irin yarda da aminci ya samu daga wajen mammina ne?,har yake iya ruskar inda take kai tsaye?,baya ga tarin dogarawan dake gadin sassan?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar dake yawo qasan ranta. "Yana da kirki da sauqin kai,amma har yanzu na kasa sabawa da ganinsa,sai na dinga jin shi dabanne a cikinmu" Akhnan ta furta a hankali da yanayin daya sanya aisa waiwayowa ta kalleta. Maida dubanta gabanta aisa tayi sannan a hankali tace. "Komai naki ya bambanta dana mutane akhnan.....ki yawaita addu'ar daidaituwar dabi'unki dana kowa......kirkinsa shine abun dubawa ba wani abu na daban ba" . Shuru tayi maganganun aisa suna dawo mata. Ita ta sani a karan kanta ba kowa bane yake iya fahimtarta ba,ba kowa bane yake iya karanta badinin halayenta ba,shi yasanya sau tari takan zabi yin shuru akan yin wasu bayanan........takan zabi yin shuru akan yin wasu maganganun. *MOMMA* Kamala gami da haiba ne suke magana da kansu a dukkan wani taku qwaya daya da zatayi zuwa kebantaccen parlor dinta da takan gana da baqin da suka kasance na musamman a wajen ta. Doguwace irin tsahon da zaa kirashi da tsaka tsaki,irin tsahon da yake qarawa mace kyau kawai bawai don ya sanyata cikin jerin sahun kyawawan mata ba. Sanye take cikin tufafin al'ada na cikakkun buzaye,tufafin da aka zamanantar dashi da wani irin sakakken dinki daya suturce jikinta gaba daya ya kuma qara mata kwarjini da cika idanu. Ko ba'a gaya maka ba kana kallonta kaga buzuwa..........irin buzuwar da ko a cikin qabilarsu da yaren nasu ma ta musamman ce ita. Farace qal kamar zaka ita hangen jijiyoyin dake kai saqon jini a jikinta.........hannuwanta da qafafunta sunsha qunshin jan lallen da ba'a masa kowanne irin ado ba,an qunsa ne bisa siga da yanayin gargajiyar da aka saba. Koda kanta yake a lullube amma hakan bazai hanaka ganin tudun sumarta dake daure cikin lallausan farin mayafin data yane kanta dashi ba. Lokacin da qafarta kuma ta taka matakale qarshe mata biyun dake tsaye a gurin kamar masu jiran isowarta suka fara gaidata. "Barka da saukowa......barka da fitowa". "Barka kade.......sannunku da hidima mamo sannunku samia" Ta amsa musu cikin kulawa da yanayin nan nata na girmama dan adam koda wayeshi. "Armelle ta iso?" Ta sake tambayarsu tana takawa a tsanake ga hanyar da zata kaita parlor din. "Ta qaraso......tadan jima tana tsimayinki ma". Wadda aka kira da mamo ta fada tana kama stairs din saman nata,don ita da samia suke kula da tsaftar makwancinta. "Yayi kyau" Ta amsa tana dokin isa ga armelle din. "A fito lafiya" Samia ta fada tana bin bayan mamo zuwa saman. "Allah yasa" Ta amsa su tana buda qofar da zata kaita ga parlor din. Babbar macace zaune cikin parlor din saman tattausan kilishin dake mamaye a parlor din. Wani irin ni'imtaccen muhalli ne maras hayaniya wanda ke dauke da kalolin peach da coffe light,tare da wani lallausan qamshin apple freshner daya wadatu dashi. Baqa ce kakkaura,wadda kana kallonta kasan ta fito ne daga qabilar Agadasawa. Sanye take da wasu irin tufafi tamkar na saqi ruwan bula me turuwa sosai da har ya sanya suka kasance masu duhu kadan. Akwai wani haske na nutsuwa saman fuskarta,tare da wata kamala da bata rasa nasaba da riqon ibada. "Barka da fitowa" Ta furta tana miqewa da ganin fitowar momma. "Barka kade armelle........zauna" Ta fadi kafin ita din takai ga zama tana mata nuni da kusa da ita. Zamewa tayi ta zauna satin qafafunta sosai tana tattara nutsuwarta. "Allah shi taya miki......" "Ya ake ciki armelle?" Ta tambayeta qagauta da jin bayanan daga bakin armelle din yana sake fitowa sosai saman fuskarta. "Altaab nu'uman ya iso masarutar nan" Armelle din ta fada a taqaice. "Alhamdulillah" Momma ta samu kanta da furtawa,kalmar data fito hade da wani nannauyan numfashi,saita maida bayanta ta jinginar ga jikin kujerar da take kai alamun samun rangwame daga duk abinda takeson ji din yana zagwanye daga fuskarta. "Armelle" Ta kirata a nutse. "Ranki shi dade". "Ina buqatar cikakken rohoto game da yadda komai zai wakana,ina kumce sauraron jin daddadan labari". *Zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *MYNITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* FREE PAGE O4 ______________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ________________________________ "In sha Allah,na miki alqawarin komai zaizo kamar a gabanki suka gana" Ta fada kanta a qasa. Kai momma ta jinjina tana jin yarda da armelle,ta tabbatar ba za'a samu akasi ba......tayi imanin komai zai tafi daidai indai armelle ce har fiye da yadda takeso. Tsam armelle ta miqe sannan ta rusunar da kanta. "Na barki lafiya" Ta juya a nutse tana takawa ta fita a parlor din. Sosai momma ta sake zuqar wani numfashin da ya cakuda da nannauyar ajiyar zuciya. Akhnan itace BARAZANARTA ta farko a rayuwa duk da ta kasance wani ruhi me tsananin daraja a wajenta fiye da diyoyin da suka fito a cikin ta. Akhnan itace barazanarta ta wani bangaren kuma itace kwanciyar hankalinta......akhnan itace matsalarta ta wata fuskar kuma nutsuwarta da kwanciyar hankalinta........shin ta yaya zata maida komai ya zamana akan saiti?,tambayar da ita kanta bata san amsarta ba. Daya daga cikin kebantattun lambunan gidanne wanda ya zama na musamman koda a cikin masarautar. Waje ne da yake da sassa biyu masu matuqar dadin zama saboda shuke shuke na musamnan dake gurin. Kusan kowanne tsiro da aka dasashi a wajen ya fito daidai da girmansa asalin irinsa daga qasar France da Germany aka kawoshi,wannan ne ya sanya zaka ci karo da tarin tsirrai wadanda sam sam baka sansu ba baka kuma sama dasu ba. Ya zama na musamman ne saboda irin wannan tsirran da yake qunshe dasu,sai ya sake zama na daban saboda tarin nutsuwa da rashin hayaniya da gurin yake dashi. Tun gabanin ka qarasa kaiwa ga lambun zakayi amannar cewa wani isashe ne a wajen......wani basaraken ko kuma wanda sarauta ke zagayawa a duniyarsa. Tarin dogarai dake tsaitsaye a kowanne dagin qafa da zakayi da kuma saukewa,cikin shiga da suturar masarautar TAHUO. Ba wanda ke motsi a cikinsu,suna tsaye ne qyam cikin son bawa yarimansu kariya. A nutse take karantar yanayinsu da yanayin da gurin ya sauya izuwashi cikin kowanne taku nata da zatayi,ta sani masarautar TAHUO din babbar masarauta ce kaman yadda tasu take.........girma dadewa da kuma yawan al'umma,saidai batajin ta kamo tasu ta fannin IZZA da QARFIN IKON da suke dashi. "Eh........ Lallai ne,da gaske ne abinda ake fada game da yarima altaab" Aisa dake takawa tare da akhnan ta furta qasa qasa daidai yadda sautin zai isa ga kunnen akhnan. Da gaske take,tsarin da yanayin ya burgeta,yanayin da ya sanya cikin jikinta takejin kamar akhnan tayi miji........kamar altaab din zai dace zaiyi kuma daidai da tsarin akhnan. Baki kadan akhnan ta tabe,saidai bata ko motsa labbanta ba ballanta tace komai da aisa. Bata jinta cikin yanayin magana,koda kuwa tana da jin cewa wani abu tasan wannan banbancin dake a tsakanin tunaninta hangenta dana sauran al'umma ya zama babbar katanga kuma hijabi daga fahimtar ma'anoninta motsinta da maganganunta. Kamar a cikin jikinsa yake jin tahowarta......kamar a cikin jikinsa yake jin alamun fuskantowarta zuwa muhallin da akayi masa mazauni,saiya daga kansa a hankali daga duban Mac book din da yakeyi,yayi kyakkyawan gani kuwa ta hanyar zube idanunsa a kanta lokacin da take takowa d'ai d'ai da qasaitaccen takunnan nata. Wani irin abu ne me qarfin gaske ya harba daga tsakiyar qirjinsa zuwa zuciyarsa........wata mummunar faduwa gabansa yayi,sai ya lumshe idanunsa can qasan zuciyarsa yana gayawa kansa. "Ka nutsu altaab". Tsahon second biyar sannan ya sake bude idanunsa yana maidawa kanta da wani irin qwarin gwiwar daya samu ya arota da qarfin cin tuwo. Ba sau daya ba,ba kuma sau biyu ba yakejin labarin kwarjinin da take dashi. Sau da dama......sau tari kuma siririyar dariya yake saki,shine fa altaab........altaab nu'uman sirreen?,har akwai dama wata halittar diya mace da zatayi masa tasiri da girma?,har akwai wata qwayar halittar KWARJINI da zata sanyashi ya gaza fuskantar diya mace ko wacece ita?,komai girma da izzarta......komai qarfin ikon masarautarsu?......kai koda hurul'eeni ce. Daga sanda girma ya ruskeshi.......shekaru suka cillashi zuwa matakin samartaka baisan adadin matan da suka soshi ba.......baisan adadin matan da yayi soyayya dasu ba.........baisan adadin matan da ya sanya kuka a kansa ba.......sai a yanzun 'yar sarkin AGADEZ zata gagareshi?. Bai santa ba,......bai kuma taba katarin ganin koda gilmawarta ba bare akai ga ganin hotonta.....wani abu daya fuskanci yana wahala shine.......sanin ainihin fuskarta da kuma kamanninta,duk kuwa da cewa SHUGABA ce kuma CEO ta babban kamfanin da kaf nijer babu na biyunsa. Babban kamfanin da ida kace baka taba sanin sunansa ba ko bakasan da zamansa ba kayi gawurtacciyar qarya. Tana da wani irin dogon tsinkaye.......iya nazari da kuma karantar komai da wani irin kaifin basira dana idanu. A yanzun da take takowa tana sake fuskantarsa kwata kwata hankalinta bai tare da aisa dake fasalta mata altaab din da yadda take tsammanin samun dukka wani quality da take buqata tattare dashi. Inda a yanayin nishadi take tabbas zata yiwa aisa murmushi ne,a yau ta yarda ta kuma sake yarda da gasken gaske ita din tasha bamban da kowa.......kamar yadda take diyar MUHAMMAD HAMMUD tallin tal! Haka dabi'unta dama zabubbukan rayuwarta sukayi nesa dana kowacce mace dama kowanne mutum. A abinda baifi taku goma ta riskeshi ba ta gama tantance altaab.......ta kuma tabbatar cewa YA FADI bazaici ba ba kuma zai tsallake sharuddan da take neman ya cikesu kafin ya samu nasarar mallakarta ba. Duk da cewa tana qare masa kallo ne amma koshi da ake kalla din bai fahimci shi take kalla ba......tsaiwarta a gabansa ya sanya wani abu tsarga masa tun daga qasan tafin qafarsa har zuwa tsakiyar kansa. Hakanan ya samu kansa da miqewa da dan hanzari,ya miqa hannu yana jifanta da murmushi,ya dawo da daya daga cikin kujerun dake wajen daura da tasa yana fadin. "Barka da fitowa......marhab". Har yanzu idanunsa na a kanta yana jifanta da wani irin murmushi hadi da sanya hannunsa ya sauke nadin rawanin daya rage bayyanar fuskarsa gaba daya zuwa qasan habarsa......murmushi da ya jima da sanin cewa,yana daya daga cikin abinda yake narkar da zuciyar 'yammata.......yana daya daga cikin abinda yake qara masa kyau tare da fidda zatinsa. Wani irin abu na daban yakeji a kanta,wani irin yanayi da bai taba tsintar kansa a ciki ba game da kowacce d'iya mace ba.......tabbas inda yasan yadda AKHANAN take.......da ya jima da nemawa kansa ita. Sai yakejin kamar daya daga cikin matan dake aljanna ce aka sauko da ita gidan duniya. "Na tsani yawan kallo" Kalamanta suka shiga kunnensa da wani irin kaifi da sautin muryar da yanayin amonta ya tilasta masa kubcewar ajiyar zuciya. A nutse ta taka zuwa wata kujerar ta daban da wadda ya ajiye mata,har qasan ranta tana jin tambayoyinsa shikam masu sauqi ne idan har zai iya amsasun,don bata jin kwata kwata zai iya shallake sharuddanta. Inda zata iya,zata zabi tsaiwa akan zama harta sallameshi,saidai bata jin hakan ya dace da darajarta da ikonta.......baqo ya shigo cikin masarautarta ya kuma zama dalilin tsaiwarta saman qafafunta. "Waye kai?" Ta jefa masa tambayar bayan ta zauna sosai cikin kujerar,ta kuma aza qafarta daya saman daya da wani irin salon zama dake sake tabbatar da izza da qasaitarta. Sauke idanunsa ya somayi akan qafafun nata,duk da ko farcenta bai samu daman gani ba amma salon zaman nata sai yaji gaba daya ya tafi dashi. Karon farko da yaji ya soma d'ari d'ari,ya kuma soma raina qarfin nasu ikon da a baya yakejin ba wata masarauta ko sultane da yakai mahaifinsa,ballantana azo Maganar 'yan'yan iko irin na nasu masarautar. Tambayar tata ta bashi mamaki sosai,ya maida dubansa saman fuskarta yana son karantar gaskiyar tambayar tata. Abu na farko da yayi tsammanin fara ji daga bakinta shine tarba........ban gajiya sannu da hanya bisa tattakin da yayi har zuwa gareta,koda ace babu gaisuwa cikin tsarinta. To amma duka ba wannan ba........shi ALTAAB ne bata sani ba?. "Da gaske bakisan waye altaab ba?.......altaab nu'......" Daga masa hannu tayi tana alamta dakatar dashi. "Ka fadi matakin farko........waye kai?" Ta sake jefa masa tambayar tana ware manyan idanunta saman fuskarsa,idanun da suka sanya gabansa sake tsananta faduwa. Yasha ganin blue eyes iri daban daban amma ba irin nata ba........yasha ganin idanuwa masu shape da launi daban daban amma banda irin nata.....natanne da gaske ko itama tana amfani da qwayar canza launin idanu?. "Na tsani kallon qurilla" Ta furta a hankali tana ware yatsunta suka zama guda biyu....... Motsin da tayi da yatsunta guda biyu kadai suka baiwa birra dake zaune daga qasa a gefanta alamar mataki daya ya ragewa altaab ya rasa damar ganawa da akhnan din. Wani abu ya hadiye fargabarsa taba qaruwa,fargabar rasata,fargabar rasa damarsa. A baya bai zurfafa da yawa haka a kanta ba,don baisan yanayinta ba baisan kuma yadda take ba,amma a yanzun da idanunshi suka gauraya a kanta sai yakejin dukka burinsa na duniya ya ta'allaqa a kanta,duk burinsa na duniya ya rataya ne akan son ta zama MALLAKINSA,don haka ya hadiye dukka mamakin da take bashi hade da wani yawu daya zarce zuwa maqogoronsa ya fara magana. "Sunana altaab dan sarkin tahoa sarki nu'uman......nine d'ansa na farko daya haifa kuma magajinsa da zai maye gurbinsa nan ba da jimawa ba in sha Allah........" Yatsunta na hagu ta kada masa,abinda ya fahimtar dashi dakatar dashi takeyi. "Ba wannan nake nema ba.......waye kai A DUNIYA........wacce daraja gareka bayan SARAUTA?.......da wanne abu kake jin zaka iya mallakar AKHNAN?" Cak komai yaso tsaya masa,saboda tambayar tazo masa a sanda bai shirya mata ba,tazo masa ne a sanda baiyi zaton akwaita ba. Dukka jarumatar da yakeji yana da ita ya tattaro guri guda,wani sashe na zuciyarsa na qarfafashi ta hanyar tuna masa. "Kaine fa wannan altaab din da mata ke kuka a kanshi.....kada ka bada maza mana altaab......kada ka bari 'yar sarkin AGADEZ tayi nasara a kanka......ka kafa tarihi.......a kuma kafa tarihi a kanka,kayi nasarar da maza da yawa da suka nemi mallakarta suka kasa kafashi. Wannan qwarin gwiwar daya samu ya sakashi sakin murmushi. "Wannan ai tambaya ce me sauqi........ko waye kuma kika tambaya koda bani ba zaki samu amsarta.........sanin kowa ne mahaifinmu babban attajiri ne daya tara mana dukiyar da bana tunanin ko dan jika a zuri'armu zaiyi wahala a rayuwa.......komai da muke da buqata an tanadeshi tun kafin haihuwarmu.......bama buqatar karatu me zurfi don mun mallaki abinda takardar zata bamu tun kafin samuwarta..........idan kika auri altaab zaki san cewa kin samu kalar mijin da yakewa mata wahala........kin taki babbar sa'ar da ba kowacce mace keda irinta ba.....". Yatsunta ta sake motsa masa,tana jin kalamansa gaba daya sun mata banbarakwai. Ita akhnan ce zata taki sa'ar mallakar altaab?.......ba altaab za'a yiwa murna ba idan har tsananin rabo ya ratso da sa'arsa cikin rayuwarta?. A iya wannan gabar taji ta kowanne fanni altaab ya gama rikitowa..... "Zaki nake nema ba kura ba.......me fita yayi farauta ba wanda ake farutowa ba.......ILIMI ina buqatar mijin da iliminsa ya kasance shine matakin qarshe na ilimi a DUNIYA......SA'A kuma tana ga wanda yayi nasarar mallakar diyar sarkin agadez.......bazan wahalar da lafuzza na ba wajen yi maka sauran tambayoyi ba.....don ka fadi tun a nan......abu na qarshe....." Ta furta da kalaman dake fita a jejjere kamar wadda ke irga adadin haruffan da zatayi amfani dasu a wajen........... Abu na qarshen da bata fadeshi ba kenan saita miqe a qasaice,tana jin kamar iya haka ya kamata ya gama jin sautinta,kamar tayi masa alfarma me yawa idan ta qara bari yaci gaba da jin sautin nata........abu na qarshen data qi gaya masa ta kuma kalmashe magananta a cikinta ta fara takawa dashi,ya bita da wani irin razanannen kallo me cike da mamaki,saidai ita dinma tana jin ya kamata maganar ta fits a cikinta.........yadda aka halicceta kenan......yadda ta dabi'anci kanta kenan.....muddin tana ji a zuciyarta ya kamata magana ta fita tana barinta ta fita,bata ajiyar maganganun da takeji sun cancanci su fita din. "Bakayimin ba......baka dace da irin tsarina ba". "Wanne tsarinne irin naki?,a shirye nake na dabi'anci kaina zuwa ga wannan yanayi da tsarin" Altaab da ya kasa zama ya miqe da wani irin sauri ya furta yana duban akhnan da bayanta kawai yake iya gani wanda ke lullube da babban mayafin dake sharar qasa wanda yazo hade da rigar. "Ka makara........kafin ka shigo da'irata ya kamata kasan wannan" Abinda ta fada kenan a taqaice,sai taci gaba da takawa tana motsa yatsarta,abinda ya bawa birra daman matsowa dab da bayanta a rusune tana biye da ita. "A fitar da kyauta mafi girma da nauyi wadda zata taba zuciyar masarutar tahou a hadashi da ita........akwai abota tsakanin mahaifinsa da sultane........ina buqatar tarin karamcin agadasawa yayi masa rakiya zuwa gida". Ta fada tana jin kamar a yau lambun yayi mata tsaho da yawa,don bata da burin da ya wuce ta kammala ficewa daga cikinsa. "An gama Allah shi taya miki" Birran ta furta cikin tsananin girmamawa. Haka kawai takejin wani nishadi yana ratsata sanda take takawa tana komawa zuwa cikin gida.......tunda ta samu ta kori altaab sai taji kamar ta zare wata qaya. Wannan nishadin nata ne ita kadai,kuma wani yanayi ne da bazai boyu a fuskarta ba,bata kuma buqatar tayi wani abu da zai sanya hadimai na gidan da nata hadiman sassauta matsayinta da izzarta,don haka ta sallami kowa ta soma takawa ita kadai zuwa nata sassan ta wata sirrintacciyar hanya data haramta kowa ya bita idan ba sultane ita ko su mammina ba. Shukokine suka lullube hanyar suka zame mata tamkar sune rufin gurin,wasu irin shukoki dake sarqafe da junansu,wannan ya bawa tsintsaye da yawa daman baje kolin samar da guraren zama gurin. Wasu irin tsintsaye da dare da rana basa gajiya da raira waqoqi da wani irin kuka me sanyi. Duk da cewa nishadi ne qasan ranta amma sam bai nuna saman fuskarta ba. Tsaki taja karo na hudu kenan,tanaso ta kawo dakatar da zuwan da maza sukeyi neman aure gurinta. Ta fara gajiya,tana kuma hangen raguwar martaba ne kawai a gurinta. Batasan rana ko lokacin da wani namiji zai samu yarjewarta a aure ba......to meye duka na batawa kai lokaci irin haka?. Sam ita bata shirya rabo kowa cikin rayuwarta ba,bata sha'awar hakan sam,don bataga abinda zasu bata ba. Hankalinta kwance ta isa ga qofar data sadata da sassanta,bata kuma tsaya ako ina ba ta zarce zuwa bedroom dinta. *_Uhmmmm........tofa😊_* zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* *LAST FREE PAGE 05* _____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ ★Yadda Armelle da take zaune a gabanta ta sadda kai cikin wani irin taushi da rashin son su hada idanu kadai ya darsa qaqqarfan zargi a ranta. Tun kafin Armelle ta bude bakinta tace komai ta soma hasashe iri daban daban,hasashen daya soma haifar da motsuwar zuciyarta da kuma soma taruwar gangamin tawagar fushi a qasan zuciyarta. Ta sani......wannan din dabi'arta ce,tana da zafi,tana da fada tana kuma fushi,saidai dukka wadannan dabi'un nata akan gaskiyar ta suke faruwa. Ba ita ta yiwa kanta wannan shaidar ba......kusan shaida ce data sameta daga wajen kowa. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Ta furta tana kuma sake zama sosai ta zauna cikin Kujerar,sannna ta ajiye carbin hannunta a glass table din dake kusa da ita. "Armelle" "Ranki shi dade" Ta amsa mata tana gaza dubanta. "Ki gayamin komai kada kice zaki boyemin". Kai sosai Armelle ta jinjina,sannan ta daga kanta a hankali ba tare data iya duban momma ba. "Shima taqi amsarsa.......taqi karbar tayinsa na aurenta". "Allahumma la sahla illa maja'altahu sahla.......la haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem" Ta fada tana qoqarin danne fushin dake taso mata. Maida kanta qasa Armelle kawai tayi ba tare data sake cewa komai da ita ba. Kowanne motsi na uwar dakinta sananne ne a wajenta da abinda yake nufi,koda bata fada ba tasan cewa fushi ne sosai yake taso mata shi yasa take maimaita addu'ar. Da alama tana qoqarin danne fushinne da nauyin addu'ar don gudun aikata abinda zai jawo musu dana sani. "Armelle.......idan na lissafa daidai wannan shine karo na goma sha daya da biftu ke aikata haka?". Kai armelle ta jinjina,tana jin tausayin momma din yana ratsata da yadda take sake dulmiya cikin damuwa cikin kowanne wucewar rana kwanaki da kuma watanni dukka akan AKHNAN din ita kadai. "Haka ne ranki shi dade.......amma dole abi abun a sannu....don......" Hannu momma ta daga mata tana dakatar da ita. "Jeki abinki armelle......kiyi haquri......nan gaba kadan zan nemeki". Tsam armelle ta miqe,tasan halin dattakonta,tasan kuma halin karamcinta,da gaske tana buqatar space dinne kamar yadda ta buqata. "Allah shi huci zuciyarki" Bata iya amsawa armelle ba,don tana jin kamar zuciyarta zata balle daga qirjinta ne ta fito. "Ki saka buhaina ta dubamin yiwuwar gabawa da sultane". Maganar tadan bawa armelle mamaki sosai. Baqon abune a wajenta ganin sultane ko kebanta dashi,musamman a irin wannan lokacin na yammaci......a kuma ranakun da yake samun yawaitar baqi qwarai fiye da kullum,amma sanin yanayin da ake ciki ya sanya bata tunasar da ita akan komai ba ta saka kai tana ficewa zuciyarta ita kanta cike da alhini da kuma dogon nazarin da taso ace momma ta tambayeta wani HASKE Ko ta shigo da ita ciki,to amma ita dimma tana tsaiwa ne kawai inda aka buqata,duk da dadewa da kuma tarin amincin dake tsakaninta da MORSA SAFIYYA(momma). Cikin kowanne bugawa da jini da kuma zuciyarta sukeyi ba abinda takeji a cikin ruhinta sai wani irin tashin hankali. Khadeeja ce?,khadeejan juhaifanta......jinin JUHAIFA ne.....jinin juhaifa ne ake waannan wasan kuran dashi?......idan ta zuba idanu gudan jinin juhaifa qwaya data tallin tal data bari a duniya ya wulaqanta haka shin TAYI ADALCI?.......anya bata zama BUTULU ba?,anya batayi cin amana ba?. Jinin juhaifa ya zarcewa duk wata kima da martaba a gurinta da idanunta......zatayi dukkan wani yaqi......zatayi kuma duk me yuwuwa na ganin bai wofanta ba. Ko sau daya ko kuma daidai da qiftawar idanu..........bata taba daukan iqirarin MAMMINA da wasa ba. Wani irin kalamai ne da suka yiwa zuciyarta kyakkyawan dashe,irin dashen da girgizarsa ko tabuwarsa ba abu bane mai sauqi. Ta aminta da dukkan zuciyarta wani babban yaqi ne ya shigo rayuwarta,tun a wancan lokacin ta sani.......jikinta kuma yake bata cewa akwai wani shiryayyen abu da zai iya faruwa,ko a kusa ko a nesa........sai gashi a nesan da bata taba kawo irin wannan nesan ba. Duk yadda zuciyarta ke bata shawarar ta zauna ko zata hutar da qafafunta ko hakan zai kawo sassauci ciki rai da gangar jikinta amma ta kasa. Tana jin mintunan da aka diba kafin ta samu amsar yiwuwar ganin me martaba din kamar sunyi wani mugun tsahon da suka kusa daidaita da tarin watanni. Kasa juriyar ci gaba da tsaiwa cikin falon tayi,don haka saita matsa da dan zafi zafin nama ta sanya lausasan takalmanta ta gyara lullubin dake saman kanta sannan ta soma fita a parlor din. Barka da fitowa hadimanta suke mata cikin sadda kansu qasa,ta daure zuciyarta qwarai wajen ganin ta amsa musu yadda ta saba,duk da cewa ruhinta da gangar jikinta ba yana a tare dasu bane sam sam. "A dubomin buhaina a duk inda take.........a gaya mata ta shaidawa sultane ina nan ina sauraron ganawarmu" Morsa safiyya ta fada tana hade tafukan hannayenta guri daya,cikin qoqarin controlling abinda takeji yana mata kaikawo a zuciya. "An gama" Nanay ta fada,Daya daga cikin hadimanta dake da wani irin zafin isar da saqon morsa safiyya din. Wata nannauyar ajiyar zuciyar ta sauke tana janye jikinta da idanunta daga jikin window din,wanda yake tuna mata da abubuwa masu tarin yawa da suka shude. Daidai lokacin da hadiman guda biyu ke shigowa buhaina da nanay. Daga bayanta suka zube cikin girmamawa kamar yadda suka saba,sannan buhaina ta fara magana. "Allah shi riqa miki.......me martaba sultane yana cikin baqi masu yawa.........duk da kusan da yawa ya sallamesu........amma gajiya bana tunanin zata barshi ya ganki a dai.........". Wani irin suka maganarta ta yiwa zuciyar morsa safiyya,zafin daya ratsa zuciyarta ainun. Ba al'adarta bace ganin sultane barkatai irin haka ba........hasalima ita da sultane din akan dauki kwanaki uku ba tare data sanyashi a idanunta ba,duk kuwa da cewa miji yake a gareta kamar yadda mammina take mata a wajensa. Lokuta da dama a duk sanda zata buqaci ganinsa a irin wannan yanayin,tana yin hakanne bawai don buqatar kanta ko wani kebantaccen abu da ya shafeta ba,kusan dukka buqatar ta mutum daya ce wato akhnan,duk da cewa a idanu da zuciyoyinsu basa kallon hakan akan buqatar kansu face buqatar qashin kai. "Daga wanne lokaci zai iya shiga lokacin taqaitaccen hutu?". Saida buhaina tayi qasa da kanta sannan ta amsa mata. "Nan da mintina biyar zuwa goma ranki ya dade". "A daukomin rigar waje" Tayi umarnin tana soma takawa a hankali tana nufar qofa,abinda ya gaya musu cewa tana da buqatar fita kenan. Ba jimawa mariya ta dawo da rigar da sassarfa,ta rusuna tana yafa mata,yayin da morsa safiyya ta qarasa sakawa sannan ta qarasa lullube jikinta da wani irin yanayi dake nuna zafin da takeji a zuciyarta dama jikinta gaba daya,suka fara takawa suna ficewa ita da mutum uku cikin hadimanta. Duk taku daya da takeyi tana fuskantar sassan sultane zuciyarta qara zafi take mata. Kusan bayyanarta a wajen a irin wannan lokacin wani irin baqon abune da ba'a saba da ganinsa ba. Mutum ce ita da zaka dauki dogon zama cikin masarautar baka sanyata cikin idanunka ba......mutum ce da zaka jima a cikin masarautar bakaji tace komai dangane da komai ba.......idan nace komai ina nufin umarni hani ko kuma zartaswa. Kaf ta tattara hankalinta da rayuwarta ne dama duk wani ikonta a kan gidanta KADAI. takan fadi lokuta da dama idan ta zauna hira da hadimanta. "Ba kowanne abu bane yake da buqatar kayi magana sharhi ko tsokaci akai ba. Wasu abubuwan zaifi kyau kayi shuru a kansu,domin shurun yafi zame maka ado kima da Kuma kwarjini hadi da cikar kamalarka a rayuwa". A tare da ita sun koyi abubuwa masu yawan gaske,a tare da ita sun dauki wani irin darasi da babu shi a kowanne sashe na duniyarsu. Kanta tsaye ba kuma tare da jiran umarni daga dogarawan dake da wani irin shiga tsari da horo na musamman ba,wadanda ke tsaron qofar da zata sadaka da kebantacciyan parlor da yafi kama da wata fada me zaman kanta ta doshi qofar kai tsaye,abinda ya tilastawa duk wani wanda yake gurin janye ganinsa kame kansa da killace ganinsa daga kanta. Koda ita din ba daya daga cikin matan dake da daraja ta farko cikin qasar agadez ce ba.......ita din ta musamman ce,da wata irin kamala da kwarjini da sassanyar nutsuwa suka yiwa tufafi. Tana da wani irin girma a zukata da kuma idanunsu.......tana da wani irin matsayi da KAME KAI da tsame baki daga dukkan al'amuran da basu shafe ka ba dama wadanda suka shafekan suke siyawa dan adam. Ba su kadai ba.......su buhaina dukka da ta taho dasu suma nan din shine qarshen inda aka lamuncewa takawarsu,don haka ita kadai ta tsoma qafa a palace din da ta kebanta ga sultane muhammad hammud da kuma iyalinshi a halinsa. Hankali kwance,cike kuma da wani irin nutsuwa ta fidda kayan jikinta ta musanyasu da wasu kaya da birra ta ajiye mata. Dogon wando ne leggings me bin jiki sosai,sai gown dinsa me dogon hannu data zauna das a jikinta ta kuma bude sosai daga qasa. Birra tasan zabinta,kusan tana cikin mutum na uku data gama sanin komai da take so,duk da har yanzun ita kanta tasan tabar birra dinne kawai ta san abinda taso ta sani din. Sassan nata babu motsin kowa,domin kuwa sanannen abu ne.......mutum ce ita ba koda yaushe take da buqatar mutane a kusa da ita ba,wannan ya sanya dukka hadimanta suke tsananin kiyayewa da dukkan abinda suka san bata so,domin ita din zuciyar SULTANE ce,HASKEN AGADEZ kuma. Hankali kwance ta zaba ta kuma nutse cikin jerin sofas din dake parlor din,sai a lokacin hankalinta ya koma kan wayarta,don tayi imanin wannan matsalar ta gama da ita kuma. Ta sani......bawai abun ya qare bane......bawai za'a tsaya iya haka bane.......amma har cikin zuciyarta take gayawa kanta da kanta zata yiwa tufkar hanci.....zata kuma daqile afkuwar hakan a nan gaba. Ta gaji da ganin fuskokin mazan da suke nuna kansu a gabanta. Mazan da zuwa yanzu ba zata iya riqe lissafin adadinsu ba,har yanzu tana ji a ranta BASU KAI BA,wannan alfarmar tata har yanzu ba wani DA NAMIJI da ya samu nasarar taka koda matakin farko na samunta. Sashen adana lambobi ta nufa(contact),taci gaba da dubawa a nutse da wani irin aji daya zame mata dabi'a koda ita daya ce a waje. Haleesha shine sunan data tsaya akai,ta kuma danna kira sannan ta sanya wayar a handsfree tana ajiyeta a hannun kujerar kamar yadda kusan dabi'arta ce hakan. Ba kasafai take sanya waya a kunne ba......muddin hakan ta faru lallai duk wanda take magana dashi din wani mutum ne muhimmanci qwarai da gaske a wajenta,kamar sultane mammina aisa shehinaz da ire irensu. Bugu biyu rak aka daga wayar daga daya sashen,saboda sanin illa barin kiran ya zama miscall da zai iya jawowa mamallakiyar number. "Barka da yammaci Madame......" Aka fadi da sautin dake nuna tsananin girmamawa. Sai da taja fasali tana duba dogayen yatsunta,ta lumshe idanunta sannan ta budesu kafin tace "Ya kike haleesha?" "Ina lafiya Madame" Ta amsa cikin jin dadin nuna qanqanuwar kulawarta a kanta. "Yayi........an kammala karbar designs din?" "Eh Madame......ke kadai ke jira". Kai ta jinjina,tana jin zuciyarta da hankalinta gaba daya ya koma niamy "Wannan tafiyar ce ta kawomin tsaiko......amma ina hanya gobe in sha Allah". Kai haleesha ta jinjina tana mamakin dawowarta da wuri. "Allah ya kaimu Madame.....don sosai kasuwa take buqatar kayanmu". "Tout se passeda bien in sha Allah(komai zai daidaita in sha Allah,zan kum duba demande(request) da kika turawa enterprisé". "Je vouse remercie Madame(na gode madam)" Haleesha ta fada cike da farinciki. Bata sake cewa komai ba ta gintse wayar,ta maido hankalinta cikin falon tana furzar da siririyar iska daga bakinta. Ita kanta tana mamakin yadda take jin qirjinta wasai,duk da lokaci lokaci tana dan jin tunanin yadda sultane zai tunkareta da batun hambarar da lamarin altaab da tayi,duk cewa tasan bata da wata matsala ko damuwa game da sultane....don duk abinda takeso shine cikar muradinsa......amma ita din bataso ta sanyashi ko yaya yaji ba dadi akan wani mutum da bata jin darajarsa da d'ara ko ina ballantana ya zama silar sosuwar ran sultane. Irin so takewa sultane da mammina.......wani irin tattalin muradi da kuma farincikinsu takeyi. Murdinta na cika burinsu akan duk abinda suka sanya interest akai daban yake a zuciyarta......sai kuma akayi katari su din suka kasance mutane ne masu fifita maslaharta da muradinta akan nasu. Waya ta jawo,ta saka wasu taqaitattun lambobi don yin kira bangaren hadimai da bayi,wanda cikin qasa da mintina biyar birra ta bayyana. "Ki duba dressing room.......a canza min luggage sababbi na gaji da yawo da wadannan.........karki sakamin komai a ciki sai inner wears din da mammina ta aikomin dasu da sleepwears......suna cikin wani LV Luggage........gobe inaso muyi fitar sassafe.......ki shaidawa manu.......banaso nayi sallan azahar sai a niamy". "Angama ranki shi dade" Ta fada tana yin qasa da kanta sannan ta yunqura ta miqe. Har birra din tayi gaba akhnan ta sake kiranta. "Je voudrais un verre de lait,s'il vouse plaît(ina buqatar cup daya na madara)" Kai birra ta jinjina a hankali sannan ta juya zuwa can wani sashe na daban da freezers din ke jere kamar an haliccesu ne don kawai su bautawa buqataun akhnan. Tana ciro madarar data kasance zallar madarar shanu ce lafiyayya me kyau,duk da wasu lokutan tafi amfani da nonon raqumi da akan tatsoshi musamman saboda ita daga lafiyayyun raquman dake masarautar. Wasu irin raquma ne masu daraja da tsada,saboda irinsu na musamman ne da zai wahala ka samesu ayankin nijer idan ba gidan iko irin masarutar agadez din. Tana mamakin yadda fiye da rabin rayuwarta ta dogara ne da shan madara nono da 'ya'yan itatuwa. Qwarararrun Cuisiniére(cook) ne da ita da suke qarqashin jagorancin mutum guda da akullum sukan bata awanni kawai don shirya mata abincin da zata ci wanda zai burgeta,saidai kusan dukkan a wannin nan sukan tashi a banza,don abinda zata tsakura taci din zakayi tsammanin yau ne ta fara koyon cin abinci. Sunyi hannun riga da qiba ballantana kuma tumbi,saidai kuma madarar da ta abota ta taimaka mata qwarai wajen samun wata irin lafiyayyar fata tsadadda da skin care product din take amfani dashi suka taimaka wajen bata wani nau'in kala na musamman koda cikin fararen matan ma,gefe guda kuma da murjajjen jikin dake da wani irin shape da ake kira da qirar cocacola ko kuma qirar kalangu a hausance. Sai data ajiye mata komai da take buqata sannan tace. "Kina da buqatar wani abune ranki ya dade?,ko kina buqatar su bushira su zama kusa dake?" Kai ta girgizawa birra,don a yanzun kadaicewa kawai take da buqatar yi ta shaqi iskar data cakuda da iya numfashinta ita kadai. Kada kan ya bawa birra amsa,saita juya a girmame tana fita don cika umarnin data bata dazun. Sallamar mammina ta sanyata ajiye kyakkyawan glass cup din glass din dake hannunta da aka yiwa wani irin ado da launin gold dake sake tabbatar da sarauta zallarta. Miqewa tayi tsaye tana jiran qarasowar mammina din tare da qoqarin karantar yanayinta don sanin dame mammina tazo din. Kadan kadan fargaba nason rabarta......tana da tabbacin mammina ta samu labarin tayi rejecting altaab........batasani ba ko altaab din yaso ya zama zabin mammina amma tayi rejecting nasa?,tana tsoron hakan ta kasance kuma ya zama silar bacin ran mammina din. Sai data sake matsowa kusa da ita sannan ta fahimci kadaran kadaham fuskar mammina take,wannan yadan bata sukuni kadan,sukunin daya sanyata fara takawa ta ruski mammina din ta kuma aza kanta saman kafadarta tana sauke ajiyar zuciya. "Don Allah mammina......don Allah kada kice altaab kinso ya zama zabina". Sakanni uku mammina ta dauka,sannan ta dora tafin hannunta saman kan akhnan tana shafawa a hankali. " Har abada zabinki shine nawa.......har abada ba zamu tilastaki ko mu tursasaki zuwa ga auren wani ba.......namu shine mu nusasheki,idan kin aminta muma yayi mana......idan baki aminta ba muma baiyi mana ba.......amma saidai......" Mammina ta qarashe fada da wani irin sanyi a muryarta,sanyin daya Sanya akhnan daga kanta daga kafadar mammina din tana kallon cikin qwayar idanunta. Girgiza kai akhnan ta fara yi a hankali. "Morsa safiyya?" Akhnan ta fada tana son gasgata hasashenta. Kai mammina ta daga a hankali cikin alamun nuna d'ari d'ari,sai kuma ta kama hannun akhnan din ta jata zuwa saman daya daga cikin kujerun ta zaunar da ita ita kuma ta zauna a qasa a kuma gabanta hannunta cikin na akhnan har yanzu. Da wani irin sanyi taci gaba da magana murya qasa qasa. "Banaso morsa safiyya taci gaba da zargina.......banaso taci gaba da yimin wani kallo na daban.......banason wannan alaqar.......wannan dangantakar da naketa qoqarin gyarata tsahon shekaru taci gaba da wargajewa......" "To idan ya wargaje sai me mammina?.......me yasa kike abu kamar kina tsoronta ne?" Akhnan ta fadi tana ware manyan blue eyes dinta akan mammina,alamu na soma tasirantuwar bacin rai suna bayyana qarara saman fuskarta. Da sauri tahau girgiza kai "Kul akhnan,kada na qara ji kada ki qara fada,ko kin manta morsa safiyya mahaifiyarki ce?". Musawa akhnan keson yi amma bataso tayi jayayya da mammina......saida kalmar MAHAIFIYA akan morsa safiyya ta kasa zama daidai cikin zuciyarta. " Mahaifiya daya mutum keda ita a rayuwa da duniya......kuma ni kece mahaifiyata" Tayi maganar dukka wata fara'a dake saman fuskarta tana bacewa bat. Kai mammina ke girgizawa. "Banaso akhnan......banason wannan furucin.......banason wannan dabi'ar akan morsa safiyya.......biftu......ya kamata ki gane tana qara nesantani da samun hadin kawunanmu". Wani dunqulallen abu akhnan ta hadiye,ta dauke kanta daga duban mammina zuwa gefe. Batasan me yasa mammina ke batawa kanta lokaci ba,batasan me yasa mammina ke damuwa da son samun yarda da aminci matar ba. Bata taba ganin soyayyar mammina cikin idanun matar ba,duk da yadda ita din ke qoqarin ganin ta kaucewa abinda duk zai bata ranta. Bata taba ganin damuwa da damuwar mammina cikin lamuran matar ba......bata taba ganin alamun morsa safiyyan zata taba duba zuwa ga buqatun mammina ba ko sau daya ne tak!. "Ni ke kadaice momma na.....ko zan daina fadin komai wannan bazai gogu ba" Akhnan din ta fada can qasan muryarta. Dan qaramin murmushi mammina ta sake tana sake kamo hannuwan akhnan sosai cikin nata. Wani abu guda daya daya gaza sauyawa daga hali da dabi'ar akhnan......tun daga haihuwa zuwa yau data zama cikakkiyar mutum shine KAFIYA DA TAURIN KAI. Wasu dabi'une da suka kasance mata abokai tsakanin ruhi da kuma rayuwarta...wasu dabi'u da kowa yasan cewa wasu rubutattun abubuwa ne cikin jininta. Idan tace EH babu wani abu dake sauya EH dinnan har abada......hakannan idan tace kuma A'AH shima babu wani abu dake da qarfin ikon canzata har gaban abada. Koda kuwa hakan yana nufin samuwar wani abu da zai zame mata qalubale ko lalura,dabi'ar da ita kadai hajiya zaitun ke iya dealing da ita......daya daga cikin abubuwan daya sanya sultane ya sake sallama mata. *ME KARATU?* *WACECE HAJIYA ZAITUN(MAMMINA?)* *WACECE MORSA?* *MEYE MATSAYINTA GURIN AKHNAN?* *MEYE MATSAYIN MAMMINA A GURINTA?* *WAYE LU'U LU'UN NAN?* *WAYE ZAI CIKA DUKKA WADANNAN QA'IDODIN DA KUMA DOKOKIN NA AKHNAN?* *WAYE WANNAN TAURARON?* *_WADANNAN SHAFUKAN BASU WUCE TABA KA LASHE KO D'AN D'ANO BA KADAI,DON SUNYI KADAN QWARAI SU HASKA MAKA ME LABARIN LU'U LU'U YAKE QUNSHE DASHI_* *TURKA TURKACE ME TARIN YAWA........MATSANANCIN KAIDI DA ZAZZAFAR SOYAYYAR DA BAMUSAN A CIKI MEYE ZAIYI NASARA BA* *IZZAR.....QASAITAR....... MULKIN......TUGGUN...... MAKIRCIN KO KUMA ZAZZAFAR SOYAYYAR LU'U LU'U?* *KARKI KUSKURA KIYI SAKACI KI KUMA YI GANGANCIN DA ZA'A BARKI A BAYA CIKIN TAFIYAR NAN* *_HAJIYOYINMU MASU JIRAN NA FISABILILLAHI 😂😂😂.......HAJJAJU BA GIRMA A ABUN......DON ALLAH 700 DAI BA ZATA GAGAREKI BA.....KI ZAMA ME CAPACITY MANA,DA KUNYA KULLUM A GANKI A GIDAN ALLAH YA BAKU MU SAMU😂,zoki siya naki ki ki shigo discussion group namu da capacitynki,aikin wuce a siya asanmiki_* *ina taya wadanda suka siya nasu murna.....ina me basu tabbacin tafiyar bata wasa bace......zamu lula zuwa DUNIYATA in sha Allah* *na gode.....na gode* zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *MASU BUQATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU QOFA A BUDE TAKE......AMMA TALLA NE BISA TANTANCE INGANCIN ABINDA KAKE SAIDAWA BA SHACI FADI BA* 08187255862 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 6 (paid novel 08187255862) __________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ *_MORSA SAFIYYA_* Tun a parlor din qarshe da yake mazaunin shinge na qarshe da zai kaika ga turakar sultane morsa safiyya ta samu tabbacin sultane yana ciki. Sai a sannan ta tuna wannan lokacin wani kebantaccen lokaci ne a gareshi kowacce rana ta duniya,wani kebantaccen lokaci da yakan zauna yayi wasu addu'o'i har zuwa wasu awanni kafin ya tashi. Ba bata lokaci ta murda handle na qofar dakin tana tura kanta ciki gami da sallama. "Wa'alaikumussalam warahmatullah" Ya amsa sallamar cikin wata nutsuwa da tarin kwarjinin daya kasa tsaida morsa safiyya ko ya hana bayyanuwar bacin ran daya riga yayi tasiri saman fuskarta. Cikakken ba'abzine ma'abocin tsaho da qibar da za'a iya kiranta da sunan murjewar jiki kawai. Sanye da jallabiyya 'yar qasar Morocco wadda tadansha banbam da sauran jallabiyya da aka saba gani,saboda bayan zubin dinkin morocco da akayi mata,kana dubanta zakasan farashinta na musamman ne saboda qasaitattun mutane irin me martana sultane muhammad hammud din. Shigowarta bai sanyashi ya fasa shimfida lausassar fara dardumarshi ba,duk da hakan bai hanashi ganin tasirin fushin data shigo dashi ba. Wani lokacin yana ganin SAFEENA a tare da ita........saidai ba safeenan bace. Akwai tarin abubuwa da banbamce bambance daya saka tazara ya kuma shata layi tsakaninta da safeena din. Yayin da wasu gamayyar halaye da jini kar d'arsa tsakanin mutanen da JINI ya zama sanadiyyar amsa sunan DAN UWA yake haifarwa. A qasaice ta samu kanta da takawa,tana kuma sake tsuke fuskarta wajen qoqarin bayyanar da dukka fushinta. A wannan lokacin a wannan karon bata jin zata iya......bata jin zata iya kauda fuska tayi kamar komai faru ba......batajin zata qaryata feelings dinta da abinda ke tasowa tun daga qasan maqoshint har zuwa saman harshenta. "Barka da yammaci" Ta furta muryarta a cushe guri daya. Da zuzzurfan kallon nan nasa ya bita,kallon da tabbas ta jishi har cikin jininta,to amma ba zata yarda ta kallo kwarjantattun qwayar idanun nan nasa dake hana mutum duk wani motsi da yayi niyya ko ya kamata yayi ba. Muryar safeena ce..........amma safiyya ce tayi magana.......kamannin safeena ne amma kuma dabi'un na safiyya ne........safiyyan ce dai,da wannan sautin da wannan fusataccen yanayin nata daya tabbatar ba zaa kwashe lafiya ba a duk sanda ta shigo dashi. A nutse yake qare mata kallo,yana son tuna kwanakin daya dauka bai sanyata cikin idanunshi ba. "Barkanki......kina lafiya?". "Magana nazo muyi dakai" Ta fadi kanta tsaye ba tare data tsaya damuwa da amsa tambayar lafiyarta da yayi ba,hannuwanta kuma goye a qirjinta,yayin data kauda kanta wani sashe na daban ba tare data yarda ta kalleshi ba. Kai ya jinjina,ta iya rigima da gasken gaske,irin rigimar da idan ta farata sai abinda hali yayi. Wata irin birkitacciya ce ita idan bataso ba,birkicewar da shi kansa a wasu lokutan yake kasa gaza shawo kanta. "Allah yasa maganarki bata shafi khadeejatu ba?" Ya furta maganae da qwarin gwiwar da fushinta bai karya shi ko kassarashi ba ko kadan. Har batasan sanda ta sauke hannayenta da sauri ba ta kuma maida fuskarta zuwa sashen da yake........yanayin sautinsa kawai ya tabbatar mata da gaske indai akan khadeejatu ne ba wani magana da zata tasirantu a ransa?.....kamar ma launin sautin nasa yana gaya mata tabar batun kan khadeeja karta sakoshi. "Saboda idan a kanta ne baka da lokacin da zaka saurari safiyya?......saboda idan a kanta ne baka da sauran wani qwarin gwiwar jagoranci?" Tayi masa tambayoyin a jere tana zube masa kyawawan idanuwan nan nata da shekaru basuyi nasarar jirkitasu ba sam,idanun da yake hango tsantsar kamanninsu dana biftu dinsa(akhnan),idanun da sau tari kallon cikinsu suke sanyashi dagewa morsa safiyya qafa,saboda akwai wasu tarin kamanni masu daraja a cikinsu. Qaramar cushion chair dake daura dashi me wani irin yanayi dake nuna alfarmarta ya jawo ya zauna akai cike da wani irin tarin nutsuwa,ya sake zuba mata dukka idanunsa yana kallon ta na wasu daqiqu kafin yace. "Ba duka abinda kika lissafa bane.........ina nufin hakanne kawai don har yanzu ba wani abu guda daya da khadeejatu tayi wanda ya sabawa addini". "Al'ada fa?" Ta sake tambayarsa a zafafe,duk da yadda idanunsa ke mata kwarjini sukeson dakusar da kaifin fushinta. Sake tsareta yayi da kallo kafin ya dage kafadunsa biyu. "Har a al'adar ma banajin ba daidai bane" "Koda gudun aure ne?,da kore duk namijin da yazo da buqatar aurenta komai cancantarsa?" Tayi maganar a karo na biyu cike da qwarin gwiwar jin ta riqi hujjar da a yau zata dankwafar da duk wani dalili da sultane ke iya bayarwa don samarwa da akhnan din kariya. Dif din da yayi da yadda yaci gaba da kallonta kawai ba tare da yace komai ba ya soma bata hope........ya soma bata fata akan sultane,ya kuma soma bata yaqinin a wannan karon saita balla wannan shingen.......wannan iyakar don gano ainihin meye a shirye a bayanta?. Ga mamakinta murmushi sultane ya saki yana dan lumshe manyan idanunshi da akhnan tayi gado,ya dora hannunsa ya shafi tattausar sumarsa ta asalin abzinawa sannan ya maida bayansa ya jinginar da kujerar. "Shin musulunci ya haramta bawa diya mace daman zabar miji ne?.......ko ya haramta zabar mijin da zaiyi daidai da daraja da martabar mace?". Sak tayi kawai tana dubanshi.......wani bacin rai sabo yana sake taso mata gami da qara ninkuwa a ranta. To ta ina sultane muhammad hammud ya cika sarki.......gwarzo kuma jarumi me wata irin madaukakiyar daraja a suna kawai bare akai ga nagarta........amma tabbas a nan FADUWARSA take........tarannan da akace dan adam yake bai cika goma ba.......anan tashi rashin cikar take. Zuciya dama gangar jikinta gaba daya sukayi rauni. Yana kima ta miji a gurinta......yana da martaba ta shugaba a cikin qasarsa......yana da daraja ta shekaru daya bata. Dukka wadannan suna bidar gurbinsu a gurinta......dukkansu suna bidar muhallinsu a dukka kalamai da aikinta......amma kuma hakan yana nufin tayi shuru ta bari ayita yin abinda take jin ba daidai bane?. Hakan na nufin ta zuba idanu BAKI yana yawa akan abinda tayi imani shi kadai zai fita kusa dashi?,hakan yana nufin ta bada dama komai yaci gaba da wanzuwa a bahaguwar hanya?. Kowa ma yasan ba daidai bane ga WANDA yasan daidai.....wake da qarfin gyarawa cikin wadanda ke hangen rashin daidai din SAMA DA ITA?. "Wannan shine alqawarin?......wannan shine tabbacin.....wannan shine alwashin......wannan shine cika buri wa gawar SAFEENA?" ta fada da wata irin murya data daki sultane a tsakiyar kansa. "Hasbunallahu wani'imal wakeel" Ya furta yana watsa yatsuntsa saman fuskarsa kamar wanda ke gudun ganin wani abu. "Safiyya!" Ya kira sunanta da wani irin yanayi yana sauke hannunsa daga saman fuskarsa. Duban da yayi mata daya ta karanci launin idanunsa dana fuskarsa ya sauya........hakan takeso,ta taba wani guri dake zuciyarsa........ko hakan zai sanya yayi abinda ya dace?. "Me kikeso?" Ya sake tambayarta kai tsaye. "Ka kira biftu.......kayi mata fada irin fadan da kowanne uba zai yiwa 'yarsa.......ka datse wannan halayyar.........ka kawo qarshen wannan wasan,Coupe le jeu.......ka tsaida wasan da takeyi da rayuwarta dama dukka damarmakinta.......wasan da nayi imani da yaqinin wulwulata akayi a tsakiyarsa ba tare data ankare ba.......ban yarda da zaitun ba......bazan taba kuma amint......." Da sauri ya daga mata hannu "Ça suffit!(ya isa!)" Tsaf ta tsareshi da kallonta......ba abinda ya kawo wannan dakatarwar ta gaggawa sai kiran sunan mammina a ciki da tayi. "Kada ki dauki zunubi......kada ki dauki alhaki akan abinda baki da hujja......me kikeso?" Yayi maganar muryarsa na sanyaya,sam ba zakace sarki muhammad hammud dinnan bane me yawa kwarjini. *_AKHNAN_* A hankali mammina ta bude baki da zummar sake magana,amma taba qofar parlor din data kasance ta glass ta katseta. Dukkaninsu suka maida dubansu ga qofar,kafin muryar barra'u ta ratso ta tsakanin curtains din. "Ayimin afuwa ranki ya dade keda gimbiya......" Duk da barra'u ta katse musu magangunu masu muhimmanci da sukeyi,amma saita saita muryar ta da yanayinta tace mata. "Fadi abinda yake tafe dake". "Me martaba sultane ne yake son Gimbiya yanzu yanzu a shiyyarsa". Ba mammina ba.....hatta da akhnan maganar ta bata mamaki. Abune me wahala sultane yayi aike takanas a irin wannan lokacin......ya buqaci ganin akhnan,ganin ma kuma ita kadai?,duk da suna kebewa sosai a lokutta da dama suyi hira irin na tsakanin 'ya da uba,amma yanayin wannan kiran yasha banban da kowanne. Kai mammina ta gyada. "Saqonsa ya iso,tana tafe" Ta amsawa barra'u wadda amsar mammina ta sakata matsawa tabar gurin. Dubanta ta maido kan akhnan,wadda ta jima tana kallon mammina kamar tana neman sanin dalilin kiran da sultane din yake musu ta saman fuskarta. "Anya ba wani abu matar can taje ta gayawa sultane ba?" Akhnan tayi maganar da wani yanayi da zai tabbatar maka jikinta ya bata akwai wani abu daya faru. "Ita din uwa take a wajenki.....kada ki munana mata zato.....tashi ki amsa kiran sultane". Kai akhnan ta shiga girgizawa. "Babu inda zani saida ke mammina........banajin qwarin gwiwar tunkarar sultane a yau ni kadai". Duk yadda taso ta kwatantawa akhnan bata fahimta din ba,har sai data aminta suka miqe tare akhnan din na riqe da yatsun mammina cikin nata. Cikin qasa da second biyu yanayin fuskarta ya sauya yana sake gauraya da wani irin bacin rai. A kowanne motsi kuma a kowanne taku mammina ba zata taba qyale biftu ba?.....a kowanne taqi na rayuwa ba zata taba barin komai nata ya wanzu shi kadai ba?. Wannan kawai ya isa ya bata amsar cewa.......rayuwar biftu din tana cikin wata da'ira ne da ake sarrafa mata ita ga zaton ita ke sarrafa kayarta. Morsa safiyya itace mutum ta farko da idanun akhnan suka sauka a kanta. Ta janye blue eyes dinta da bacin rai ya sanya suka sake shanyewa tana maida dubanta ga sultane dake zaune saman lallausar dardumarsa yana jan carbi. Tasha kwatanta inama ace morsa safiyyan wata mutum ce ta daban,ba irin mutanen da ko yaushe mammina da sultane ke jaddada mata girman kowanne lamari daya shafeta bane?......ba shakka da hakan zata kasance sunanta shine a sahun farko cikin jerin sunayen mutanen da zata furzar dasu daga rayuwarta. Daidai da bugawar daqiqa guda......wannan dangantakar ta UWA da aketa kiranta tsakaninta da morsa safiyya bata taba jinta ba,hasalima inda zatace wani qin jininta takeji sosai yana disa saman zuciyarta a kowanne motsi to batayi qarya ba. Tamkar bata ganta zaune a wajen ba,ta taka cikin wata irin nutsuwa da izzar sarautar dake yawo a jininta ta sanya ta zauna mata,take kuma qara mata kyau da haiba matuqa,ta qarasa gaban sultane a nutse ta sulale tana duqawa saman qafafunta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 07 __________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ Duk da kasancewarsa mahaifinta.......mahaifin da tafi kusa dashi akan kowanne d'a namiji.......akan kowacce halitta ma dake duniya,to amma ita dinma bai fasa yi mata kwarjini ba. Wannan kwarjinin da kowanne talaka dake rayuwa qarqashinsa yake ganinsa......yake dukansa itama takanji haka game dashi lokuta da dama. "Barka da warhaka sultane" Ta fadi har yanzu kanta yana qasa "Barkanki dai biftu.....ina fatan kin wuni lafiya?" Ya fada cikin tsananin nuna kulawa da kuma tausasa harshe. Yanayin daya sanya wani abu ya tsayawa morsa safiyya dake duban akhnan a wuya......duba na bacib ran yadda ta dauketa. A lokuta da dama,a yanayi irin wannan.......tanayin abubuwan da a kullum take sake sauke darajarta ne daga idanun mammina. Daya daga cikin wasu abubuwa data tsana.......bata da matsayin da har yau akhnan zata gaidata sai bisa umarnin sultane ko ita kanta mammina. Bata jin zafi idan sultane ne ya sanyata.......amma tana jin tsananin quna idan umarnin gaidata ya zama ya fito ne daga bakin mammina. "Ranka ya dade barka da yammaci" Mammina data qaraso ciki ta fada a hankali tana me zamewa saman lallausar dardumar dake shimfide a dakin,da wani irin zama dake nuna zallar ban girma,tamkar irin zaman da bayinsa keyi a gabansa. Idanunshi ya dago yana dubanta "Barkanki zaituna.......fatan kin yini lafiya?" Wani murmushi ta aje tana gyara zamanta sosai sannan a ladabce ta sake magana. "Lpy alhmdlh......hakan kuma ya sake tabbatuwa a kanmu sakamakon naka wunin cikin aminci da qoshin lafiya" Kai ya jinjina a hankali,qaramin murmushi yana subuce masa wanda ya bayyana har saman labbansa. "Ma sha Allah......ya kacaniyar jama'a". "Har mun kaika ne ma Allah shi tayawa mulkinka?,kai ya kamata a yiwa wannan tambayar" Ta qarashe maganar tana sakin murmushi. Dole Shima ya maida mata sannan ya amsa. "Alhamdulillahi bisa taimako da jagorancin ubangiji". " Ma sha Allah,Allah ya qara lafiya ya qara taya maka" "Allahumma ameen" Ya amsa a taqaice yana aza idanunsa akan akhnan "Ga mommanki nan" Sultane ya fadi yana dan duban morsa safiyya sannna ya maida dubansa ga akhnan. "Barka da yammaci" Akhnan din ta fadi ba tare data daga idanunta ko tayi wani abu da zai nuna morsa safiyya take gaidawa ba. Cikin tsananin juriya da shanye abubuwa kaman yadda ta saba ta hadiye wani abu,muryarta can qasa kuma a shaqe ta amsa mata "Barka" Daga hakan sai wani irin kakkaifan shuru ya gifta,kafin sautin muryar akhanan ta sake motsasu "Papi(kamar yadda wasu lokuta take kiransa idan tana buqatar UBA da zasuyi magana),na samu saqon kira daga gareka,ina fata ya kasance lafiya?" Murmushi kadan ya saki,ya ajiye tasbahar hannunsa yana sake bada hankalinsa a kanta. "Khadeejatu" "Na'am papi" Ta amsa tana sake yin qasa sosai da kanta. "Altaab yazo dan sarki nu'uman haka ne?" Kai ta jinjina "Yazo papi" "Kun gama ganawa?" Ya jefa tambayar kai tsaye. "Mun gama,har ma ina tunanin zuwa yanzu yayi nesa da masarautar AGADEZ". "Ma sha Allah.....yayi miki?,kina jin zaki iya zama dashi kiyi masa biyayya a matsayin mijin da zai kaiki aljanna?". Sultane muhammad hammud ya fada yana ci gaba da nazartarta. Shuru ya ratsa na daqiqa daya zuwa biyun da basu haura biyar ba......daqiqar data wuce da bugun zukatan morsa da mammina........zukatan dake kwance qirazan da suke da mabanbantan burika da hasashe dukka akan AKHNAN din. "Baiyimin ba papi......na kuma bayyana masa sannan na sallameshi" Ta fadi kanta tsaye cikin gwada daya daga cikin dabi'unta na fadin gaskiya kai tsaye ba tare da wani qumbiya qumbiya ko ado ba. Shuru ya danyi yana wani nazari. Nazarin da yafi karkata kan rashin haramci cikin abinda ta aikata. Aure zama ne na mutum biyu da dukkaninsu suka aminta zasu rayu da juna har zuwa mutuwa.......ba wata yarjejeniya bace ta taqaitaccen lokaci.....ko kuma taron da zaa yishi tsakanin wasu awanni a gama a watse ba. "Shikenan.......Allah ya tabbatar da abinda yafi alkhairi". Maganarsa ta qarshe da tayi daidai da saukar wani nannauyan abu a kunnuwa da zuciyar morsa safiyya......kalaman "Ameen ameen" Da suka fito daga bakin mammina kuma suka sake gwamutsa tunaninta daga wani yanayi zuwa wani bigire na daban. "Zan iya tafiya idan an yarjemin?" Akhnan ta furta cikin neman izini. "Mommanki nason yin magana dake itama" Ya fadi yana mata nuni da morsa safiyya. "Da d'iyata kadai nakeson nayi magana baya gakai dake cikin dakin" Ta furta cikin wani irin yanayi da zai nuna alamu nason nuna mallaka da kuma isarta. Dukka su ukun suka zuba mata idanu suna dubanta. Yanayin da tayi magana kadai wani irin sauti ne dake tafe da izza da nuna taqama. A Hankali mammina ta yunqura ta miqe tana furta. "Bismillah". Tsam akhnan ta miqe itama tana gyara zaman yafen dake saman kanta,wanda santsin gashinta ya hanashi zama dai dai. "Ina zaki?,mommanki keson magana dake fa?" Mammina ta fada tana duban tsakiyar idanun akhnan. "Ba wata magana dake da muhimmanci idan babu ke a cikinta........babu wata magana da zata bada ma'ana muddin akace an cire uwa daga rayuwar d'anta......". "Khadeejatu" Sultane da ya miqe daga saman daddumarsa ya koma saman daya daga cikin kujerun ya kira sunanta. Waiwayowa akhnan tayi tana duban sultane din ba tare data iya amsa kiran da yayi mata ba. "Ki koma kiyi magana da mommanki kamar yadda ta buqata". "Rabu da ita......ka qyaleta,khadeejatu qaramar yarinya ce?......idan kin manta irgen shekarunki ya kamata ki koma baya ki tariyosu da kyau!" Morsa safiyya tayi maganar a zafafe da bayyanannen fushin da sultane da kansa zaice ya jima bai ganshi haka ba. "Zanyi maganar kamar yadda kika buqata a gabanta......bazan kuma fasa fadin duk abinda nake da niyyar fada din ba...........ke diya macace gajeriyar rayuwa gareki......damarmakinki gajeru ne......mafarkanki basu da tsaho......burikanku kuma qayyadaddu ne.......kina da taqaitaccen lokacin da idan kikayi wasa dashi saikinyi kuka da idanunki........a sanda kukan nan bazai amfana miki komai ba. Waye UBANKI da kike ganin kowanne namiji ba tsaran aurenki bane AKHNAN?!!!" Ta qarashe maganar da madaukakin zafin daya tokare mata dukkan wata mashaqar numfashi da kuma iska data hada maqogaronta da hunhunta. "Idan an kutsa cikind duk wani sassan dake daukan sauti zuwa kwanyarki......an miki busar ke din d'iyar da tafi kowa ce to KIN CUCI kanki........idan a baya kedin yarinya ce.....yanzu cikakkiyar mace kike da takai minzalin aure daidai da daidai..........karki manta uwarki ba kowa bace tamkar BUZUWA kamar kowa........hakanan mahaifin daya kasance shine taqamarki......zaki tsufa a sanda mazan da kika raina sukayi miki nisan da baza suji kiranki ba harma su waiwayeki..........zaki tsufa a sanda su suke tsaka da sharafinsu da kuma ganiyarsu......" Saita juya inda mammina ke tsaye. Wani irin fusatacce kuma wulaqantaccen kallo ta watsa mata. "Naso ace zan iya bar miki akhnan kiyi yadda kikaga dama da rayuwarta.......saidai kuma girman maganadisun jinin SAFEENA dake kewaya a jikinta bazai barni na iya hakan ba.........bugu da qari UWA ake iya barwa D'A.......ba muna UWA ba.......akwai da dama da basusan ciwon haihuwar ba.........amma suna da zarra irin ta nagartattun uwaye........AMSA SUNA ta sigar da sunan yazo dashi wata baiwa ce da ba kowa Allah yake baiwa ba......." "Safiyya!......" Sultane ya kira sunanta da wani irin sauti daya sanya kalamanta lanqwashewa ba tare da sun gama fita gaba daya ba. Waiwayowa tayi tana dubansa da birkitacciyar fuskarta. "A gabana kuke.......sassauci na da bayar da dama ga iyalina bawai yana nufin kowa yayi irin maganar da yaga dama ba" Yayi maganar da irin harshen daya dawo mata da hayyacinta,ya sake jadda kalmar SULTANE ne a gabanta har tsakiyar kwanyarta. Sadda kanta tayi qasa a sanyaye tana tattalin hawayenta. Alqawari ne wannan.......alwashine wannan na haramtawa kanta kuka a gaban zaitun HAR ABADA. "Tuba nake.......amma dukkanku abun kiwo ne.....kuma zaa tambayeku game da abinda aka baku kiwon". Lafazinta na qarshe kenan ta juya tana barin dakin da hanzarinta. Tamkar suka haka yaji lafazinta na qarshe yana sauka saman tsokar zuciyarsa,ya lumshe idanunsa yana saukesu saman fuskar mammina da hawaye suna fara sauka daga ramin idanuwanta zuwa saman fuskarta. "Bansan me zan yiwa safiyya na burgeta ba.......bansan me zan yiwa safiyya na amintar da ita ba,dama nuna soyayya ga wani jinin yana iya zama qiyayya babba irin haka?". Mammina ta fadi muryarta na wani irin rawa,ba muryarta kawai ba hatta da hannuwanta. Sosai akhnan ta kamo hannuwanta ta riqe cikin nata,wani irin matsanancin fushi yana tasirantuwa tun daga cikin idanuwanta zuwa saman fuskarta. Me yasa matar nan sam bata da kirki?,me yasa baa taba zaman lafiya da ita?,me yasa kullum burinta ta wulaqanta ta kuma tozarta mammina?.....me yasa koda yaushe idanunta a kulle suke bata ganin alkhairi?,wanne irin butulci ne wannan?......shin bata jin kunya da nauyin yiwa mammina GORIN HAIHUWA a koda yaushe muddin magana me shigen haka zata hadasu? "Mammina......." Tayi maganar muryarta tana rawa. "Ki daina kuka mammina s'il vouse plaît(please),ina tare dake koda cikin wanne irin yanayi ne......ke din uwata ce,babu wani abu sa zai canza wannan" Ta qarasa maganar tana jin zafi sosai cikin ranta. Tana jin wani mugun haushin morsa safiyya......tana ji inama koda sau daya mammina din ko sultane zasu bata daman yin wani abu......yin wani motsi me kama da hukunci akan morsa safiyya......tana jin har ranta ta cancanci hukunci.......butulcinta kuma me girma ne. "Barni nayi kuka biftu......qyaleni nayi kuka akhnan..." "Saboda me mammina?!.....saboda me zakiyi kuka?,baki cancanci kiyi kuka ba.....morsa safiyya ita ya kamata tayi kuka bake ba.....!!!" Tayi maganar a zafafe fiye da dazu,tana kuma nuna qofar da morsa safiyya ta fita. "Khadeejatu" Sultane ya furta da wani raraunan sauti da sam bai dace da yanayinsa ba. Wani irin mutuwar jiki yakeji tana ratsashi da wani rashin karsashi sam,tun daga sanda momma tayi maganan qarshe ta kuma fice......sai ya zamana kamar ta fice da kuzarinsa ne da karsashinsa. "Zo nan ki zauna". Ya fada yana nuna mata gefensa. Sai data zauna sannan ya dubi mammina itama " Zaitun ya isa haka......samu guri ki zauna" Kai ta soma girgizawa tana sake sharce hawayen dake sake bulbulo mata. "Kayi haquri......ba wai ina nufin nayi gardama da umarninka bane......amma ina jin cewa bai cancanci na zauna ba alhalin na saka zuciyar safeera a cikin qunci ba.......tabbas kome safeera ta fadi inajin kaman daidai ne.........tana da iko,tana da puissance(power) akan akhnan sama da tawa........ina tsoron fushinta kada yayi tasiri a kanmu......anya Allah bazai tambayemu ba?" Ta fadi da wata narkakkiyar murya dake nuna zallar tsoro da kuma fargaba. Sosai abinda ke takore a wuyan akhnan yake sake fadada.......tana jin kamar zatayi aman zuciyarta. Ta kasa buda baki ta sake cewa da mammina komai,sai lumsassun idanunta da taketa juya manyan qwayar idanunta a ciki. Me mammina tayi da Allah zai tambayeta da haqqin morsa safeena?. "Zoki zauna tukunna" Ya sake fadi yana nuna mata guri. A hankali take takowa harta iso inda yake nuna matan,saidai kamar kowanne lokaci......bata taba hada mazauni dashi ba,muddin yana tsaye ita tana tsugunne,idan yana tsugunne ita tana zaune,idan yana saman kujera ita din bata da wajen zama sai qasa,daya daga cikin abubuwan dake qara martabarta a idanunsa kenan. "Akhnan.........kinfi kowa sanin morsa mommanki ce......don wani tsohon karatu ne da na tabbatar tun bakisan me kalamaina ke nufi ba kika haddacesu.....zan sake maimaita miki morsa mommanki ce......biyayya a gareta ya zama dole a kanki kamar yadda zakiyimin......kamar yadda zakiwa mammina" "Qwarai kuwa" Mammina din ta fada tana goge fuskarta da hancinta da gefen lallausan mayafinta. "Kije ki bawa morsa haquri........ki mata alqawari.......ki saka kuma a ranki zaki maida hankalinki ki fidda mijin aure". Kai mammina ke jinjinawa,jin sultane ya dakata ya sanya a nutse ta soma magana. "Gaskiya ne.......a nan morsa ta fimu gaskiya ta kuma fiki gaskiya,kaman yadda naji tasha fada miki mutuncin mace dakin mijinta......cikar mutuncin mace shine aure,komai gatanta da martabarta........don Allah akhnan......ko don nayi haske a idanun morsa,ta daina tuhumata,na daina shiga zarginta ki tsayar da wanda kikeso......raina bayamin dadi......zuciyata bata min daidai" Ta qarasa maganar tana hade hannayenta alamun roqo muryarta na rawa kamar wani kukan yana dab da zuwan mata. Kai kawai take jinjinawa don bata da abinyi sama da haka. Akwai tarin maganganu da tarin ra'ayoyin da take buqatar furtasu ko qirjinta zai rage nauyin da yayi......amma a yanzu ba abinda take buqata sama da kebe kanta ita kadai. "Allah yayi miki albarka........ya baki abokin rayuwa na gari" Sultane ya fadi idanunsa akan diyar tasa da wani irin qauna da kulawa me dimbin yawa. "Ameen ya rahman ya Raheem" Mammina ta fada cikin tsantsar kulawa. *Zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 08 ______________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ A nutse ta miqe tana takawa,tana kuma jin yadda bacin rai yake dawainiya da ita,tana lissafa yadda zata iya zuwa wajen morsa safeera tace ta yafe mata.........tana juya yiwuwar hakan,saidai kuma muddin umarnin sultane ne,ba wani abu dake canza wannan umarnin,ba a gurinta kadai ba.......umarninsa TABBATACCEN ABU ne da babu damar saba masa canza masa ko guje masa. Har ta kusa da qofa ta dakata,ta waiwayo da wata irin kasala "Papi" "Na'am" Ya amsa mata yana dubanta,sai tayi qasa da kanta da salo na girmamawa. "Inaso ayimin izini gobe na koma Niamey" Shuru ya danyi na wasu sakanni,wanda hakan zai nuna maka nazari yakeyi kafin yace "Allah ya nuna mana......Allah ya tsare" "Godiya nake" Ta fada da lallausar muryarta sannan ta taka ta soma ficewa. Sanda ta bacewa ganinsu mammina ta dauke idanunta daga bakin qofar tana maidawa kan sultane,Shima ita yake kallo. Lokutta da dama tausayinta yana tasiri a ransa fiye da qauna da kuma soyayya. Rashin haihuwa a duniya wani irin ciwo ne da bashi da misali. Jarrabawar zaitun kenan.......yana daya daga cikin abubuwan daya kawo kyautatawa me dimbin yawa tsakaninsa da ita......baya ga wata irin tarin biyayya da take masa tamkar siyanta yayi a mazaunin baiwa bawai matar aurensa ba. Yana da qwayaye biyu a duniya da zai nuna yace nashi ne.....mallakinsa ne......mammina bata da ko guda daya,amma koshi da ya mallaki qwara biyun cikin bege da kewar samun masu yawa yakeyi. "Ranka ya dade......me yasa ka yarje mata?,me yasa ka aminta ta koma Niamey tun a gobe gobe?,baka tunanin zata koma ne taje ta zauna ita kadai tayita tunani tana sakawa kanta damuwa?". Idanu ya zuba mata na wani dan lokaci kafin ya janye idanunsa. Irin wannan kulawar da qauna me yawan gaske yake gani a idanun mammina akan akhnan tsahon shekaru ashirin cif kenan. Har yanzu kuma baiga abinda ya canza wannan damuwar qaunar da kuma kulawar ba. "Zuwa yanzu ya kamata ki rage sanya kanki a damuwar al'amuran akhnan.......ba biftun ki ta shekaru ashirin baya bace......wannan wata biftu da muke sanya ran aurar da ita nan gaba kadan,ta kuma bamu jikoki masu tarin yawa" Yayi maganar ta qarshe yana jin kwadayin son aurar da ita yana taso masa. Yana tsananin son yara.....yayi burin tara iyali masu fadi da girma......saidai hakan bai samu ba......tashi rubutacciyar qaddarar kenan. "Ita din wani sashe ce na zuciyata kamar yadda nasan sashe ce ta rayuwarka.......bazan taba iya daina qaunar biftu ba har gaban abada,don Allah ka tayani baiwa morsa haquri" Tayi maganar fuskarta na narkewa alamun zuciyarta ta karye sosai. Hannunsa ya miqa ya riqo nata a tausashe,cikin salon son kwantar mata da hankali yake dubanta. "Baki laifin komai ba zaitun.......kawai safiyya nada zafi.......tana da fushi......wannan ne tazara da banbancin dake tsakaninku......amma bata da riqo,bana tunanin abun zai dade". Kai mammina ke girgizawa,wani abu yana mat yawo cikin zuciya. "Ka tayani fahimtar da ita.......ya kamata ta sassauta fushinta a kaina......indai akan qaunar biftu ne.......muddin kulawa da yawan adadin soyayyr da nake gwadawa biftu zata iya zama laifi......ka fahimtar da ita zanyita dawwama a mazaunin me laifi a wajenta" Tayi maganar tana riqe hannun sultane da kyau,wani hawaye me dumi yana zarto mata. Hannunsa ya miqa a hankali yana qoqarin kauda hawayen daga fuskarta. "Ba zaki taba zamowa me laifi ba.....don ba inda qauna ke jawowa qiyayya.....ko bata fuskanta yau ba.....koda bata fuskanta gobe ba tabbas wataran zata fahimta". kawai matsawa mammina tayi ta dora fuskarta saman kafadarsa tana sakin wani boyayyen kuka daya sake daga hankalinsa. Gaba daya ranar zuciyarta a quntace take,a quntacen kuma cikin fushi da bacin rai ta qarasa yinta. Don tunda ta isa sassanta raji wani abu me kama da ciwon kai ya saukar mata,saita sallami kowa ciki harda cooks dinta dake hada hadar ganin sun shirya abincin da zasu burge uwar dakin nasu dashi a wannan ranar. Duk da cewa babu tabbacin fitowarta cin abincin a kowacce rana,amma hakan bai sanya sun gaji ko sun daga qafa da tunanin girka abinda zai burgeta ba. Sun sani yardarta da amincinta idan mutum ya samu cikin masarautar agadez to ya taki babbar sa'a a rayuwa,wannan ya sanya basa wasa da duk wani abu daya shafeta ko ya danganceta. Lamo kawai tayi cikin duvet,tana jin kamar wani irin zazzabi zazzabi yana son kamata,wanda ta tabbatar zallar bacin raine kawai dake sasaqar zuciyarta. A gajiye ta zare jikinta daga cikin duvet din,ta zuro dogayen kuma dogayen qafafunta qasa cikin jin kasalar miqewar kafin ta tattara dukka sauran qarfin da ya rage ta yunqura a nutse cikin yauqinnan nata daya cakuda da yauqinta na halitta A hankali take takowa gaban balcony din sassanta wadda aka qawatata da wani irin yanayi na lafiyayyun shukoki masu bada ni'imtaccen qamshe. Furanni ne masu yawa a jikinsu da suka bada launin fari da pink,abinda ya sake qawata gurin kenan sosai ya kuma bada wani launi da yanayi da musamman. Wata gown ce a jikinta ta wani irin yadi na musamman da aka yiwa sassauqan dinki,saidai gown din ta saukar mata sosai ta rufe har saman qafafunta,duk da bata da wani hannu na kirki ko kuma hannun azo a gani. Tsaye tayi jikin qawataccen qarfen balcony din,tana jin yadda sassanyar iskar yammacin ke kadawa da wani yanayi dake saurin cire damuwa aran dan adam. Sosai irin wannan iskar take mata dadi,wanda mafi yawan lokaci anfi samunta ne tsakanin sallar bayan sallar asuba zuwa yammaci da farkon dare irin wannan,yammaci zuwa daren da damina ta soma sauka a wasu maqwaftan qasashen da garuruwan,wanda gari zai hada hadari ya kuma bada iska me kyau me cakude da qamshin qasa. Sosai ta zuqi iskar tana kuna fesar da ita ta hanyar hancinta dake zaune das saman fuskarta da wani irin zubi da tsari daya qarawa fuskartata matuqar kyau. Hannu ta sanya ta janye gashinta dake yawo saman fuskarta sakamakon busawar iskar data maida gashin nata kamar wani abun wasa,don babu ribbon ko band ko daya data kama gashin dashi,hasalima tana jin kamar ciwon kai zai saukar mata ne,wannan dalilin ya sanyata barinsa a haka kawai. Tana samun view me kyau na masarautar agadez a irin yanayi irin wannan.......tana samun damar kallon cikin masarautar da kyau dake qawace da wasu irin qananun fitilu masu tsananin haske da suke sake qawata idanun me kallo,su kuma sake qawata masarautar da qara mata kyau da kwarjini. A karo na hudu ta sake maida gashinta gefan kunnenta saboda yadda yadda iska ke sake kwasoshi kaman zai shiga mata idanu. Ta sauke ajiyar zuciya me nauyin gaske tana jin yadda zuciyarta da kwanyarta gaba daya suka gaji da wannan tunanin. Tana jin kamar daren yayi mata tsaho zuwa wayewar garin da zata bar agadez zuwa Niamey.......tana jin masarautar duka ta mata zafi,sai ta dinga jin me yasa ta zabi kwana a agadez ba Niamey ba?. Ta soma jin gajiya sosai cikin dukka tunaninta,har yanzu kuma ta gagara gano amsar nan guda daya dake wahal da tunaninta. Me zatayi da aure?,me zatayi da wani d'a namiji?,bayan bata rasa komai ba?,ba abinda kuma take da buqata?.......bata jin kuma akwai ranar da zata buqaci wani namiji a cikin rayuwarta. Ba komai cikin halittar d'a namiji face zallar sonkai....... Mugunta,rashin imani ga mace da kuma tsananin son juya mutum da mulkarsa ta duk hanyar da suka dama. Ita dukka wadannan abubuwan bata shirya tunkararsu ba.......bata shirya zama qarqashin umarnin wani ko hanin wani ba........bata shirya zama qasan juyawar wani ba.......bata shirya karbar umarni ko hani daga hannun wani ba. Ita ke umarni.......ita ke hani......ita ke alfarma......yardarwa wani ya zame mata miji yana nufin dukka wadannan damarmakin sunbar hannunta. Kai ta girgiza a hankali,tuna wannan kawai yana sanya ranta ya baci,ina ga ace ya tabbata a zahiri hakan ta kasance?. Sam bata ga inda zata ita rayuwa a hakan ba.......ita akhnan ta zama qasan mulki umarni hani da gadarar wani ba.......mutum biyu a duk duniya taji ta aminta su samu wannan damar a kanta,SULTANE DA MAMMINA. "Gata na sameta a balcony.........okay to yayi ba damuwa" Ta tsinkayi muryar aisa daga bayanta. Batayi wani yunqurin waiwayawa ba tunda tasan aisa din zata iso,sai kawai taci gaba da kallon farfajiyar dake gabanta,tana kuma jin yadda muryar aisa ke sake kusanto inda take. Cikin qasa da minti daya saiga aisan a kusa da it,still dai wayar take amsawa. A jikinta takejin idanun aisa din a kanta,ta kuma gama fahimtar suna magana ne da Shehinaz. "Bansan ta yaya zan miki bayani ba Shehinaz........da ki bari kawai saikin iso din" Aisa ta fada muryarta na nuna tasirin bacin rai kadan. "Okay......gata" Ta fadi tana miqawa akhnan wayar. Girgiza kai kawai tayi ba tare data karba ba. "Kice mata idan zuwa zatayi kawai karta wahalar da kanta zuwa agadez.......ta sameni a Niamey" Ta fadi a nutse tana sakin qarfen,sannan ta taka tana juyawa zuwa ciki a hankali. Wanda dab da zata shiga parlor din da zai gangara da ita zuwa ragowa falukanta sukayi kacibus da birra da wayarta a hannunta. Ta rusuna tana miqa mata. "Kiranki aketa yi tun dazun ranki shi dade" Sai tasa hannu kawai ta karbi wayar ba tare da ta tsaya tambayar me kiran ba. Duk yadda aisa taso tayi mata maganar abinda ya faru tsakaninta da altaab a daren akhnan taqi yarda hakan ya faru,sai zuwa washegarin ranar sanda birra ta taimaka mata ta kammala shirinta tsaf cikin wata tsadaddiyar riga da bata da taqamaimen suna......saidai tana zubi da abaya......irin abayar da yaran sakunan qasashen larabawa ke alfahari dasu,suke kuma amfani dasu a manyan bukukuwansu na alfarma. Kwallin data zizarawa idanunta da lip gloss din data shafa su kadai ne baqin abu dake saman fuskarta idan ka dauke powder din da take using na wani brand dan qasar France,jikinta na fidda unique scents dinnan nata. Komai nata natural ne.......duk da tana da son ado sosai. Tana da wani irin gayu na fitar hankali.......gayu na daban kuma na musamman me jan hankali. 'Yar gayu ce irin gayun daya amsa sunanshi,wanda hakan ya tasiranta a kanta ne saboda haka aka gineta tun tana tsummar goyonta. Daidai ba brush dinta na musamman ne......kuma designer,don yawancin lokuta takan tashi dare daya ta musanya komai nata da take amfani dashi,koda kuwa soson wanka ne zuwa new design da kamfanin dake mata wannan aikin suka fidda a shekarar ko a watan. Tana cikin amsar LV bag dinta daga hannun birra data gama zuba mata komai a ciki aisa data kammala nata shirin ta kalleta. "Komai naki ya cika akhnan.........amma duk da cikar nan da yayi akwai sauran gurbin da babu abinda zai cikeshi sai aure da miji". Blue eyes dinta masu almond shape ta daga a nutse ta zube ma aisa su. Yan miskilancin suka motsa,ta motsa bakinta kamar zatayi magana sai ta fasa,ta gyara mayafinta da yake kafadarta ta soma takawa da wata iri nutsuwa saman high hill shoe dinta,wanda saboda tsininsa ba zakayi tunanin wata halittar dan adam zata iya tafiya dashi ta dadin rai haka ba. Ba haka aisa taso ba,don da biyu tayi maganar,ba shurun akhnan take buqata ba......bude bakinta takeso tayi tace mata wani abu. Ba kasafai kake fahimtarta ba muddin bata ce maka komai ba,shurunta yana da wasu irin tarin ma'anoni da suke sanyaka ka gaza fahimtar wace ita?,ina ta sanya gaba?. Sanda ta fita dining room ma ta samu barra'u na shimfida mata tattausan farin yadi saman cinyarta don gudun bata jikinta. Yayin da bushira ke hidimar shafa mata avocado da dafaffen qwai cikin bread din da zataci,kasancewar bata cin bread haka zallarsa gudun qiba. Tana da mugun son lafiyarta,tana qaunar lafiyarta sosai,don haka bata rabo da dukkan wasu nau'ikan abubuwan gyara jiki da zasu dawwamar mata da lafiyarta kyan jikinta dama kyan fatarta. Akwai nau'ikan motsa jiki da takanyi duk safiya irin wanda suka dace da mata dake qara fidda musu shape dinsu,su kuma tsayar da boobs dinsu da sauran sassannin jikinsu. Komai bushira ta gama shiryawa ta ajiye a gabanta,ta matsa kadan tana ajiye wayarta a gefe ta jawo plate din tana duban buhaina. *zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 09 ____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ______________________________ "Banji kince komai ba game da ranar juma'an data wuce" Ta qarasa maganar tana daukan mug din coffee da aka zuba wadatacciyar madara me zafi tayi sipping a hankali. Qasa tayi da kanta,tana jin qirjinta yana bugawa. "Naso nayi miki bayani ranki shi dade.......wannan jumma'ar ba'a samu damar gudanar da sadakar ba,ganin a gaggauce kike da kiran da sultane yayi miki" Har takai spoon bakinta ta maida ta ajiye tana duban buhaina din da wani irin kallo. "Me kika ce?" Ta tambayeta tana ritsata da idanu,saita sake yin qasa da kanta. "Kiyi haquri ranki shi dade" Akwai bacin rai sosai cikin idanunta take duban buhaina dasu. Sadakar juma'ar ta zame mata tamkar wani bangare na ayyukanta na duk sati. Sau tari ita da kanta take shirya kayan abincin cin wani kyakkyawan wando babba sosai na kaba,a fita dashi gidajen da basu da hali a ajiye maka a qofar gidanka ba tare da kasan daga ina yake ba. Wani alqawari ne data daukarwa kanta muddin numfashinta.......wani sashe ne na abinda yake faranta mata rai a duk sanda tayi hakan,ba tare kuma da tasan abinda yake sakata wannan farincikin da nishadin ba. "Kinsan muhimmancin aikinki kuwa?.....menene hadin kiran sultane da wannan aikin buhaina!?" Ta jefa tambayar tana dan buga cokalin hannunta kadan. "Ki gafarceni uwar gijiyata.........nayi kuskure......" "Ba kuskure bane wannan ganganci ne!" Ta sake fada cikin fadan da yake damfare da yadda zuciyarta ke a bace tun jiya. "Ammm.......buhaina......a samu a maida madadin ta juma'ar da bayi ba wannan lahadin.......nan gaba kuma kome akeyi ko meye ya faru ki dinga qoqarin ganin anyin.......idan ya kama da akwai qaqqarfan dalilin da zai hana ayin saiki sanar tunda wuri". Aisa ta karbe maganar don bataso tayi tsaho,ta fuskanci idan tayi tsahon kowa ma sai ranshi ya baci. Dogon tsaki taja ta miqe tana daukan tissue,ta tura kujerar baya tana fita daga tsakanin table din. Jakarta birra ta dauka tabi bayanta,yayin da aisa ta girgiza kai kawai taja wata kujerar ta zauna tana cewa buhaina ta hada mata abincin dan kadan,don tasan zata samu lokacin da zata gama cin abincin harta rusketa,don tasan tabbas ne saita shiga ta yiwa sultane da mammina sallama. Kai tsaye sultane ta fara gani,yayi mata addu'o'i sosai sannan ya rufe da cewa. "Ina buqatar zuri'a me yawa wadda bayanta bazai yanke ba.......zuri'arta ba zata samu dogon zango da kuma dogon tarihi ba saita tsatsonki da tsatson suhaana,kece babba,kece bake da fata a kanki sama da suhaana........kece burina yafi zurfi a kanki biftu,kiyi qoqarin zama magajiyata ta wannan fannin ma......kamar yadda kika sharen hawayen rashin d'a namiji ta fannoni da bangarori da dama.....nagartaccen suruki akhnan.......nagartaccen lu'u lu'u nake buqata.......wanda zai maye min gurbin da na rasa.......kafin ki sake shiga ko ina......ki shiga wajen mommanki kiyi mata sallama". Ya qare maganar yana tuna yadda safiyya ta kasa zama,ta ratso tsananin duhun daren jiya ta iskoshi a sassansa. Sunyi maganganun da suka tsaye masa a rai,maganganun da suketa yaqi tsakanin zuciya da kwanyarsa,suna son zaqulo masa ainihin inda matsalar da damuwar suke......sunason bashi tabbacin akwai kuskure ko babu?. Sosai maganganun sultane suke mata yawo saman kanta lokacin da take takawa zuwa sassanin morsa safiyya. A nutse take kurbar dafaffiyar madarar dake cike da wani mug dake iya baka damar ganin abinda yake cikinsa. Cikin wannan tsaren gidan da kamalarta ta qara masa kaifi. Daga qasan qafafunta daya daga cikin hadimanta ne ke zaune sanye da kayan aikinsu,daga gefanta wasu irin plastic robber ne guda biyu. Dayan wani ruwa ne da momma din ta cire qafafunta daga ciki me launin kore,dayan kuma wasu ganyayyaki ne shimfide a ciki masu dumi sosai,dumin da ko daga gefe kake kana iya fahimtar hakan,wani qamshi na daban suka hadu suka bayar,ruwan da kuma ganyayyakin. Gangar jikinta ce kawai zaune a wajen,amma dukka wani hakali nata da nutsuwarta basa wajen. Tun daga daren jiya sanda take fitowa daga sassan sultane bayan ta tabbatar sunyi magana ta fahimta tsakaninta dashi,take takowa ita daya zuwa sirrintacciyar hanyar da zata dawo da ita zuwa sassanta. Gilmawar wani abu ta gani wanda inuwarsa ta gifta ta gabanta sakamakon hasken qawayayen dake a bayanta suka cillo inuwar zuwa gabanta. "Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Ta furta tana qoqarin danne tsoron daya taso mata. Tana da halittar tsoro a cikin zuciyarta kamar kowacce halitta ta dan adam,saidai kuma macace me wani irin dakiyar zuciya jarumta da kuma juriya ainun,wannan ya bata qarfin gwiwar juyawa don ganin meye haka me fadi ya gifta ta bayanta nesa kadan da ita. Taku uku tayi baya tana komawa zuwa inda tafi tsammanin ta nan abun ya wuce. Sannu a hankali ta hangi rigar dake bayyana mata daya daga cikin hadiman dake aiki sassan mammina ne. Koda ta sake matsawa sosai sai idanunta suka soma dauko mata fuskar tamim wanda yake sake turata cikin hular qarfen dake saman kansa. Cak ta tsaya tana dubansa daga tsakanin wasu shukoki da suka kerewa tsahonta sanda yake yunqurin fita daga hanyar zuwa qofar da zata sadashi da ainihin harabar sassan nasu daga nan kuma ya bulla zuwa makekiyar farfajiyar jakadunsu dama jakadun sarki. Cak ya tsaya ya kuma waiwaya bayansa,yayi 'yan dube dubensa na wasu sakanni sannan ya sanya kansa da sassarfa yana ficewa. Kimanin sakanni talatin cif tayi a wajen kafin ta motsa ta koma zuwa hanyar da zata sadata da ainihin sassanta. "Me tamim yakeyi a shingen da ba wanda yake da hurumin shiga idan ba JININ sultane ba?......shiyyar data zama kebantacciya kuma mallakar iyalin sarki?. Gabanta taji ya fadi sanda wani tunani ya yanko mata. Hankalinta taji yana neman tashi saboda tuna yadda wancan watan akayi shari'a tsakanin bayin dake aiki a sassan mammina da kuma bayi maza dake wata shiyya daban ta gidan. An samu case na alfasha tsanin baiwar mammina guda daya.....wanda har takai ga samun ciki a tsakaninsu. Ba sultane kawai ba da baya qasar a sannan.......hatta ita hankalinta yayi mummunar tashin da sai datakai ta tara dukkan hadimanta tayi kafa musu mafi girman gargadin cewa. "Duk wadda ke da buqatar aure a cikin ku ta sanarmin,ko a ina ta samu miji kuwa ni zan aurar da ita kamar yadda ake aurar da kowacce 'yantacciyar diya.........bazan daga qafa ba bazan kuma lamunci aikin alfasha a shiyyata ba......ina tsoron zunubin da zai jawo qin amsa addu'o'ina........duk wadda na sameta da wani abu makamancin haka.......bazanyi qasa a gwiwa ba wajen miqata kotun musulunci ta cikin gidannan ta yanke mata hukuncin da shari'a ta tana ba". Maganarta tayi amfani,don cikin watan mutum uku ta aurar,ta kuma basu daman ci gaba da aiki da ita ko tafiya?,dukkansu suka zabi suci gaba da aiki da ita,don babu abinda zaka rasa muddin kana tare da ita. Can wani saqo dake kebance a zuciyarta kuma sai taji ta kasa gasgata haka......haka kawai taji ta gaza gamsuwa da wannan tunanin.......a jikinta takejin wani abu na daban,abinda ta kasa gane ko hasaso meye.......wannan tuna in kuma shine yaqi barinta yake bibiyarta har a wannan safiyar. Idanunta zube saman fuskar akhnan dake shigowa da takun da sarauta da izza suka mallaka mata shi. Sanye take cikin wata irin doguwar riga da bazaka kirata baya kai tsaye ba. Don 'yar cikin tana da dogon hannu da wani irin ado daga hannun zuwa qasan rigar daga sama,yayi data saman ta kasance kamar alkyabba maras nauyi,budaddiya sosai da,wadda hannuwanta suka kasance kamar na top riga,aka cika dukka jikin rigar da wani irin ado,adon da idan ka baza fadinta sosai daga baya zai fi maka kama da adon zanen jikin dawisu,hatta da igiyar da akayi ta musamman saboda daure gaban rigar cike yake da ado da wasu irin stones masu daraja......sai wani qaramin hijab na musamman da rigar ke zuwa dashi,wanda itakacinsa wuya,wannan shi ya qarasa suturce jikinta gaba daya sai kewayayyar fuskarta data bayyana ta tsakiyar qaramin hijab din. Idan akwai wani abu guda daya dake burge morsa safiyya akan akhnan shine SHIGAR SUTURCE jiki. Ta sani,tana suturce jikinta bawai don tasan darajar alfanu da girman abinda takeyi ba,aah.......tana suturceshi ne saboda girman kai taqama da alfahari da takeyi da jikin nata. Tana kishi.......tana kuma alfahari da kanta...... Tana martaba jikinta tare da ganin cewa.....jikinta wata kadarace me tsada da tafi qarfin kowanne kare da doki ya samu damar ganin ta a raha haka,wannan ya sanya mafi yawan suturuntu irin rigunan ne da musamman wani kebantaccen kamfani dan qasar dubai ke fidda mata su iri daban daban,sai kuma lafiyayyu lafayu masu asalin tsada da daraja. Tanason qananun kaya sosai......bata damu kuma da hijab ba bare dan kwali,amma dukka irin wannan shigar cikin gida takeyi. Sam momma ma bata tunanin akhnan din ta mallaki hijab,bare dankwali da yake zama aikin banza cikin dukkan kayanta. Duk da batasan ma'anar suturta jiki ba cikin addininta........amma ta zame mata dabi'a saboda ALFAHARINTA DA IZZARTA.......wannan din yana yiwa momma dadi......tasan kuma wani abune daga Allah wanda yake iya kimsawa bawa kyakkyawar dabi'a koda shi bawan bai kalleta a mizanin komai ba. "Barka da safiya" Akhnan din ta fada tana zama saman kilishin dake gaban momma din gami da dauke idanunta daga kan robobin da qafar momma din ke ciki. Wani abune da tun batasan ma'anarsa da muhimmancinsa ba taga momma din tanayi,har kawo yau data mallaki hankalin kanta. Ita din wata irin mutum ce da bata bari kanta yayi murfi sam......mutum ce me yawan bincike game da duk abinda zata gani wanda batasan mene shi ba. Bata yarda da jahilci ba......bata kuma yarda da rashin sani ba,bata laminci kuma kowa ya kalleta a matsayin wadda bata sani ba.......saidai kash......tana tare da wani RASHIN SANI mafi muni da batasan dashi ba. "Barka da asuba biftu,kin tashi lafiya?" Momma ta amsa da wani sassauqar murya. Baki akhnan ta tabe qasan ranta,tana dauko hoton abinda ya faru jiya tana kawoshi kusa da ranta. Kamar ba itace matar nan ba data gaggaya mata maganganu mafiya muni cikin rayuwarta ba a jiyan.....tammar ba ita bace a jiyan takeyi kaman zata qonata da ruwan zafi ba......kamar ba itace ke jifanta da mummunar fata ba?,waisai gashi a safiyar yau ta juye kamar wata hawainiya?. Sam bata jin zata ga hasken matar nan a rayuwarta kaf........kalamanta na jiya sun sake nesanta ruhinta da fatan wataqila watarana zasu fahimci inda kowannensu ya dosa. "Na tashi lafiya......zan wuce Niamey......saina dawo" Ta fadi duka a tare da sauran maganarta tana miqewa. *Zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 10 ____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ Da kallo morsa safiyya ta bita,tana jin wani abu yana taba zuciyarta sosai,wani irin qaqqarfan abu me matuqar tasiri a zuciya. "Allah ya tsare hanya......ya bada sa'a,ki kula da kanki,ki kula da mutuncinki..........ki kuma tsare martabar gidanku data mahafinki" Kusan kowanne lokaci wadannan sune kalamanta kuma maganganunta a kanta a duk sanda ta samu sukunin yi mata sallama. Bata ce komai da ita ba taci gaba da takawa tana fita......hakan kuma bai hana morsa safiyya binta da idanuwa ba har sai data bacewa ganinta. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana jin sassan jikinta suna yin wani irin sanyi. Koda wasa akace mata irin haka zai taba gwada faruwa tsakaninta da jinin safeena ba shakka zata qaryata. Da gaske rayuwa wani mafarki ne na daban. Wani mafarki ne da zuciyoyi da ruhi keyi ba tare da samun yaqinin tabbatuwarsu a sanda ake kan ginasu ba. Safeenarta.......halitta mafi soyuwa a ruhinta dama kafatanin rayuwarta gaba daya......yanzun dama akwai sanda lokaci zaizo da irin wannan yanayin tsakaninta da jinin SAFEENA?. Taja siririn tsaki aqalla ya kusa sau biyar kafin ta isa sassan mammina. Tarin hadiman dake sassan suka shiga marabtarta cikin matsanancin ban girma,saidai ba wanda ta samu amsawa. Hakan ba baqon abu bane a wajensu,musamman idan tana jin 'yan izzarta a kusa,ko kuma 'yan miskilancin suka motsa mata. Ko baya ga haka kuma dama ita din muryarta kamar wani abune me daraja a tare da ita da ba kowanne guri take sakinta ba. "Ki gafarceni.......uwar daki tana cikin muhimmiyar ganawa......bata kuma bada izinin shigar kowa ba har sai bayan ta kammala" . Bayanan tafisu ta yiwa akhnan kenan,wadda ta isa direct ga qofar kebantaccen parlor din hajiya zaitun da tasan a lokaci irin wannan anfi samunta a can. Wani irin kallo akhnan ta dago ta watsawa tafisu,tana mata wani duba na qanqanci da kuma zallar mamaki. "Hala wani abunne a kanki?.......kinsan dawa kike magana kuwa?" Akhnan ta furta cikin izzar nan tata dake bayyana cikin kowanne motsi nata. Rawa jikin tafisu ya dauka,kwarjinin akhnan din sosai ya daketa,ya kuma tarwatsa duk wata juriya da takejin tana da ita na tsaida akhnan din. "Zaki fuskanci hukunci.......tabbas zaki fuskanci hukuncin tsaidani da kuma batamin lokaci da kikayi" Ta qarasa maganar tana tura qofar,daidai sanda tafisu ta zube muryarta da jikinta dukka suna rawa. "Tuba nake.......afuwa nake nema ki yafeni......kiyimin rai". Bata ko saurareta ba ta sanya kai cikin parlor dake da qofofi biyu na musamman,ta cikin gidan da kuma wata qofar daban ta bayan ainihin ginin. "Yaya sunanshi?......." Kalaman mammina kenan da taji wanda bata ko ta kansu ba ta motsa bakinta a izzace ta saki siririyar sallama tana sauke idanunta ga faffadan mutumin dake duqe a gabanta kamar me neman gafara. "Sunan......." Ya buda baki da nufin bada amsa tambayar da akayi masa,saidai amsa sallamar da yaji mammina tana yi ya dakatar dashi,ya kuma daga kansa da hanzari yana duban me shigowar. Sam baiji motsi ko sallamar kowa ba......don haka baisan da shigowar kowa din ba. Idanu mammina ta kafeta dashi na sakannin da suka kusa biyar kafin ta sakar mata murmushi. "Karkicemin sai tafiya?" Ta fadi tana marabtarta da hannayenta,abinda ya sanyata qarasowa cikin hanzari ta zauna jikin mammina din sosai tana aza kanta saman kafadarta. "Maraba da isowa........tuba nake.... .Allah ya qara miki nisan kwana......ubangiji ya kauda maqiyanki daga duniyarn......" "Ya isa haka" Mammina ta dakatar dashi tana sanya hannunta cikin na akhnan. "Ka bamu guri haka nan......zan gana da diyata......zan nemaka wani lokaci" "An gama Allah shi biya miki" Ya furta yana miqewa da dukka tsahonsa,sannan ya sanya kai yana fita ta qofar da zata fitar dashi ta bayan sassan mammina din. Sai data tabbatar da gushewarsa a wajen,ba tare da wani motsi nasa ba sannan ta dubi akhnan. "Tun daga yanzu na fara kewar wannan diyar tawa,daya daga cikin abinda ke jefani tunanin yadda rayuwa zata kasancemin bayan na kaita gidan mijinta". Wani murmushi ya subuce ma akhnan din,murmushi nan nata me tsadar da zai wahala kayi mu'amala da ita na wasu taqaitattun lokuta ka samu ganinsa. Koda yaushe fuskarta a tsuke take,zaka dauka kaf rayuwarta batasan wani abu waishi farinciki ba. Hannunta ta zura ta bayan mammina ta rungumeta sosai. "Kune kuka takura......ku kuka matsa mammina......me nake da buqata a rayuwata bayan kun yimin komai.....kun gama min komai......sannan kun mallakamin komai". Kai ta girgiza a hankali. "Yaro yaro ne......yaro man kaza......baa nan gizo ke saqar ba.......amma na gaba kadan zaki fahimta......akwai wani abun da kike buqatar ki tafi dashi Niamey?.....bayi hadimai ma'aikata ko wani abu na buqatar rayuwa?". Manyan idanunta ta lumshe,tana jin dadin yadda take nuna damuwa da komai daya shafi rayuwarta,tana jin dadin yadda take kula da dukka buqatunta.......tasha banban da nisan tazara me tarin yawa tsakaninta da momma safiyya.........tazarar da bata jin a nan kusa akwai wani abu da zatayi wanda zai sanya ta taddota. "Babu......babu komai mammina.......saidai zanyi kewarku" Ta qarasa fada tana sake dora kanta saman kafadarta. "Muma zamuyi kewarki biftu.......amma zamu kasance ta cikin waya.........dole ne ya zame miki nauyi da kuma wajibi bawa kamfani kulawar da dukka ta dace........shine zuciyar duk wata kadara da dukiyarki akhnan........bake kadai ba.......hatta da me martaba ma". Kai ta jinjina,sannan a hankali ta zame kanta daga kafadar mammina din sannan ta miqe. Da kanta ta bude mata seat din baya,mazauni na musamman dake gareta cikin lafiyayyar motar qirar BMW X5 fara qal wadda tasha banban da kalolin sauran motoci ukun dake dauke da masu tsaronta da kanyi mata rakiya zuwa Niamey,wasu su zauna a can,nacan din kuma su dawo nan agadez sai tayi wani zuwan sai a sake canza mata da wasu cikin amintattun hadiman da masarautar agadez ta aminta dasu. "Allah ya tsaremin ke......ya kawar da dukkan wani abunqi" "Ameen mammina". Ta fada a narke kaman yarinyar qarama. Matsawa mammina din tayi tayi kissing hannun akhnan din,sannan ta maida dubanta ga aisa. " Aisa" Ta kirata kai tsaye da yanayin daba kasafai ta fiya kiranta ba. "Naam mammina" "Ki kulamin da diyata" Ta furta da yanayin dake nuna mata da gaske take. Kai kawai ta jinjinawa mammina din tana dauke kanta zuwa wani sashe na daban,kafin mammina ta matsa da baya ta rufe musu motar,suka fara motsawa kuma suna fara fita daga masarautar agadez. Duk inda zasu gifta da motocin tun daga cikin gidan har zuwa wajen gidan sai kowa ya bada hankalinsa,ya kuma matsa baya cikin girmamawa yana yi mata addu'ar sauka lafiya da wani irin ladabi tamkar tana ganinsu. Shuru motar ta dauka sanda suke nufar mano dayak international airport(AJY),inda ta saba tashi a nan,sauran hadimanta kuma su juya subi ta hanya zuwa Niamey din. Kowa da tunanin da yakeyi a ransa,saidai duk da haka waya ce a hannun aisa tana danne dannenta,wanda fiye da rabi chart takeyi ita da shehinaz da take bata tabbacin yau din ko gobe itama zata baro zinder ta shigo Niamey din. Akhnan kuwa idanunta nakan hanyoyi da shimfidaddun tituna kyawawa da suke wucewa. Cikin ranta take sake jinjinawa mahaifinta da mulkinsa,ya jawowa qasar agadez ci gaba masu tarin yawa,irin ci gaban da koda wadanda suka jima saman karagar mulkin basu samar da koda rabin rabin hakan ba. Duk da wannan nazarin da takeyi hakan bai hana zuciyarta fadawa cikin tunani ba.....abubuwa da dama dake cunkushe a kwanyarta,tana kuma tunanin hanyar warwaresu. Qaramin tsaki taja ciki ciki,a yanzu tana jin energy dinta dukka na aikinta......bata buqatar sulalar dashi da kwaranyar dashi akan wani abu can da bashi da cikakken muhimmanci ga rayuwarta,don haka saita fidda daya daga cikin wayoyinta tana jin bari ta duba sashen saqonnin email dinta ta rage yawan saqonnin da suke jiranta. Saqo na farko na biyu......ana uku idanunta suka sauka ga adireshin saqon da ya sanyata jan wani qaqqarfan tsaki da yaja hankalin aisa. Daga kanta tayi tana duban akhnan da taqi koda duban sashen da aisa din take,har yanzun idanunta nakan wayar,don haka itama aisa din saita bagarar taci gaba dayin abinda take. Tsaki na biyun data sake ja shi ya sanya aisa yin magana wannan karon,ta aje wayarta saman cinyarta ta soke yatsunta guri guda tana dubanta. "Wanda bai kashe zomon ba.....kuma ko ratayar zomonma ba'a bashi ba......na meye zaa cika masa kunnuwa?" Tayi maganar tana tsuke fuskarta guri guda. Sau daya tak ta daga kai ta kalli aisa da almond shape eyes dinnan nata dake gayawa aisa ta tara maganganu ne da yawa qasan ranta amma miskilanci ya hanata fada,sai tayi abinda aisa din tafi tsana wato maida kanta kan wayarta. Mutum biyun nan dai..... Mutum biyun nan da har kullum suke hargitsa zaman lafiyar wayarta. Zai wahala ta dauki wayarta ta gama dukka shige da ficenta a waya ba tare da taci karo da saqon dayansu ba. Ta rasa mene ne hakan?,wai tamkar ita daya ce macen da tayi saura a duniya ne?. "Babe........the pic was so hot......thanks to aisa". Cak ta tsaya tana sake maimaita karanta saqon da ya fito daga gurin naadir......haifaffen qasar nigeria da kasuwanci ya kawoshi niger din. "Thanks to aisa?" Ta karanta maganarsa ta qarshe. Jikinta ne ya bata wani abu,sai kawai ta sauka ta koma zuwa account dinta ba IG. Private account ne da ba kowa yake da ikon ganin abinda kake aiwatarwa,sai wanda kayi accepting dinsa,wanda duka duka nata mutanen da tayi accepting basu da yawa,ciki kuwa harda aisa. Kai tsaye ta wuce ga sunan aisa din,ta zarce kan abubuwan da tayi posting a dukka satin. Babban hotonta yana daya daga cikin abubuwan data saka a satin.......hoton daya samu likes da comment me tarin yawa wanda kusan mafi rinjaye da harshen faransanci ne. Hotuna ne guda biyu,guda daya nata,dayan kuma ta da aisa ne a diori hamani international airport,ranar da suka baro Niamey kenan zasu shigo zinder. Tana sanye da wata doguwar riga cikin ire iren dogayen rigunanta navy blue. Sosai color din rigar ya amshi fatarta da take jazur kaman zaka latsa hannunka jini ya fito,hakanan eye glasses din da tayi amfani dashi me duhun kala ya sake ajiye mata wani kyau na musamman,hancinta da zagayayyar fuskarta sun sake fallasa sirrin kyanta. Bata taba zaton haka rigar tayi mata kyau ba sai a wannan hoton,sai wani abu yazo ya tokare mata a wuya tana bin comments din mazan dake qasan hoton nata tana dubansu a matsayin sakarkarin da basu san ciwon kansu ba. Tarin sakarkarun kuma data bawa damar kalle fuskar da ita karan kanta wadda Allah ya mallakawa ita darajarta take gani,wannan wanne irin aikin watsar da mutunci aisa ta jawo mata?. "Me kika aikata kenan haka aisa?" Ta jefa tambayar kai tsaye ga aisa din tana haska mata fuskar wayartata me babban screen dake riqe a hannunta daidai sanda motarsu ke kutsa kai AJY. Fuska aisa ta tsuke itama,tana dinke girar sama da qasa. "Mene kuwa?,shikenan mutum bazaiyi nishadi ba?" Ta jefa mata tambayar itama tana rutsata da nata manyan idanun. Kallon aisa ta sakeyi sosai sannan ta janye wayar a tsakaninsu ba tare data janye daga dubanta ba. "Supprime ça(Delete it)" "Baiyi niyya ba" Aisa ta fada hankalinta kwance tana maida dubanta ga qofar tana qoqarin budewa jin motar ta tsaya. Bata ankara ba ta tsinci hannun akhnan saman cinyarta,ta dauke wayarta cak tana jefata cikin handbag dinta,daidai sanda aka bude mata side din da take,abinda ya hana aisa yunqurin amsar wayar kenan,don ita dinma sarautar na yawo a jininta,kuma tasan yin wani motsi ko yunquri zai iya zama abun kallo a tsakaninsu ko ya zubda musi kima. "Karki yunqurin yin wani abu mara da wayata biftu.......mallakata ce". " Idan banyi ba tabbas ban haifu ba cikin sultane" Ta amsa mata ba tare daya waiwayo ga aisa din ba. First class take zama a duk sanda tahau jirgi komai qanqantar tafiyar. Tunda kuma suka shiga din ta karanci akwai wanda ke shirin takura mata. Matashine da jin ke zagayawa a jikinsa tare da nuna zallar quruciya kudi da kuma wani sassanyan kyau. Yanayin kallon qurillarsa ya gama takurata kafin sannu a hankali ya qona mata rai,sai kawai ta fiddo eye glasses dinta masu duhu ta lullube qwayar idanunta dashi,sannan ta miqe bayanta jikin kujerar da take kai,ta kuma buda madame Bovary na marubucin nan dan qasar French Gustave Flaubert. Duk da novel din ya qunshi soyayya......amma jarumtar star din novel din,attitude nata da character nata sunyi mata sosai. Sanda jirgi ya daidaita sararin samaniya da tafiyar da bata haura awa daya ba da mintuna ta rufe novel din,tana jin yadda shauqin labain ke dibanta,amma sai ta zabi ta bawa kwanyarta wani space nayin shuru ta zauna silent don bawa kwanyarta wata qaramar nutsuwa zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *00239166221261* *Safiya musa abdullahi* *MY NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 11 Matashine da jin ke zagayawa a jikinsa tare da nuna zallar quruciya kudi da kuma wani sassanyan kyau. Yanayin kallon qurillarsa ya gama takurata kafin sannu a hankali ya qona mata rai,sai kawai ta fiddo eye glasses dinta masu duhu ta lullube qwayar idanunta dashi,sannan ta miqe bayanta jikin kujerar da take kai,ta kuma buda madame Bovary na marubucin nan dan qasar French Gustave Flaubert. Duk da novel din ya qunshi soyayya......amma jarumtar star din novel din,attitude nata da character nata sunyi mata sosai. Sanda jirgi ya daidaita sararin samaniya da tafiyar da bata haura awa daya ba da mintuna ta rufe novel din,tana jin yadda shauqin labain ke dibanta,amma sai ta zabi ta bawa kwanyarta wani space nayin shuru ta zauna silent don bawa kwanyarta wata qaramar nutsuwa. Dan qaramin blanket da aka basu tayi amfani dashi ta qarasa lullube jikinta,sai fuskarta kawai dake a waje. Ta liqe idanunta da abun rufe idanu tana juyar da fuskarta window tana sauke sassanyar ajiyar zuciya. "Biftu" Aisa ta kira sunanta a kausashe. Yi tayi kamar bata jita ba,abinda ya sake sanya aisa maimaita kiran nata har sau uku amma tayi burus da ita. Hannu tasa ta zare abunda ta rufe idonta dashi,cikin hasala tana cewa. "Don wulaqanci kina jina ina kiranki?.........ki bani wayata saikici gaba da kurmancinki ba damuwar aisa bane" Duk maganan da aisa din keyi idanu kawai akhnan ta zuba mata harta gama. Sai ta qarasa yaye blanket din kawai ta zauna sosai,ta dauki jakarta da sauran tarkacenta ta raba aisa din tana wuceta. Da kallon harara aisa ta bita,jirgin ya dauki shuru kowa yana harkar gabansa,bataso kuma tayi abinda zaiyi kiran hankalin mutane a kansu,don haka taja qwafa qasa qasa,tana tunanin meye zata mata da zai zafafeta itama ta rama?. Murmushi ya saki a hankali ganin ta koma can wani seat din daban ta narke cikin kujera tana maida blanket dinta,saidai yanzun bata lullube idanunta ba,a maimakon haka ma saita maida dubanta ga window tana ganin yadda suke keta gajimare. A nutse ya miqe yana barin seat dinsa,ya taka a hankali zuwa inda take,wanda har ya isa din bataji motsinsa ba sai daya zauna kusa da ita. "Hey cutie" Ya fada da siririyar muryarsa da kadan ya rage ta soma kamanceceniya data mata saboda zaqinta. Da hanzari ta waiwayo tana watsa masa blue eyes dinnan nata. Kallon daya saukar masa da wani irin matsanancin faduwar gaba. "Tsarki ya tabbata ga ubangiji ya furta a fili yana qarewa fuskarta kallo. Baisan kallonta daga nesa ya rage mata kyau ba sai daya matso kusa da ita. "Sunana ruslan........" Katsewa maganarsa tayi saboda wani lumshe ido da tayi gami da budesu lokaci daya,wanda suke gaya masa "Sai me?.....me ya shafeni?". "Bala'i" Ya fada cikin ransa yana jin yadda wani gumi ya fara yanko masa. Yasha ji cikin abokansa suna firar nau'ikan mata masu tsananin aji.......yadda wasu matan suka qware wajen baiwa namiji amsa da iya qwayar idanuwansu,bai taba dauka da gaske bane......bai kuma taba dauka magana da idanu kawai zata saka ka fahimci me mace ke nufi ba sai yanzu. "Ammmm.......kiyi haquri......ban nema izini ba ko?......duk da naga kamar daga daya daga cikin masarautunmu kika fito ko?". Wani abu ne yazo ya tsaye mata iya wuya,bata taba tsammanin saqon data aike masa bai isheshi haka ba....... "Baka fahimta ne?" Ta fara tana juya hannunta gamida da ware yatsun hannun. "Subhanallahi" Bakinsa ya motsa ya furta can qasan maqoshinsa yana jin maqogoronsa yana bushewa. Komai nata me burgewa ne.....me kuma daukan hankali ne.......komai nata daga kusa yafi kyau da qayatarwa.......tabbas idan yace a kowanne qarni irinta kadan Allah ke halitta cikin mata baiyi kuskure ba. Sanda yakai qarshen wannan tunanin tuni harta cusa earpiece a kunnenta,ta lullube idanunta ta kuma ja blanket dinta ta rufa har kanta ruf zuciyarta na mata suya. Bayan first class a flight batasan kuma wanne guri zata shiga ta boyewa idanuwa ba.......ashe har first class dinma an fara samun mutane marasa aji irin wannan mutumin da ko sunansa ma bata gama fahimta ba ballantana ta riqe. Ya fahimci zamansa a wajen bazai amfana masa komai ba,bazai kuma maganta masa komai ba,don haka ya miqe tsam daga gurin,zuciyarsa tana bashi shawarar ya tunkari aisa,don ya fahimci kamar ta fita sauqin kai da iya mu'amala,wataqila ta samo masa kanta. Bata ko sake bude fuskarta ba bare tasan yabar wajen ko baibar wajen ba. Har suka gama awannin da zasuyi,jirgi kuma ya saukesu a Diory hamani international airport. A nan ta taras da driver dinta da kuma security dinta mutum uku suna jiranta,wadanda suka kasance tsaffin sojoji da suka samu horo me kyau suka kuma goge ta fannin tsaro da kuma bada tsaron. Tayi zaton a motar aisa zata sake ce mata wani abu,amna sai taga bata qara cewa da ita komai ba,hasalima Mac book ne a hannunta take wani sabgar daban,sannu a hankali har suka isa unguwar tasu. Commune I,unguwa ce data kasance mazaunin al'ummar dake da sukunin rayuwa sosai koda cikin Niamey din ma. Area ce data qunshi manyan gurare,kamar ofishin jakadancin qasar amurka manyan makarantu masu tsada da daraja na 'ya'yan masu hannu da shuni da sauransu. Avenue dinsu suka shiga wanda ke cike da security dake kula da motsi da kuma kai kawo na avenue din gaba daya. Tun daga gate na farko security din dake tsaron gurin ke saluting motar. Motar masarautar agadez fitacciyar mota ce,daba wani guri da zata ratsa ba tare da ta fita daban ba. Gida me number shida anan motocin sukaci burki,basu ko danna horn ba babbar qofar da zata sadaka da farfajiyar harabar gidan me wani irin adon qarafuna masu daukan hankali dake nuna sarauta a jikinsu suka bude motocin suka shige ciki. Kusan kowanne ma'aikaci dake cikin gidan tsaye yake yana jiran isowarta,isowar data sanya kowa sake shiga nutsuwarsa har zuwa sanda birra ta bude mata motar ta sanyo qafafunta waje. "Barka da sauka.......maraba da isowa........Bienvenue chez nous(barka da dawowa gida)..........Content de vous revior(muna farinciki da dawowarki gida)". Hannu ta daga musu sannan ta juya zuwa cikin gidan hankalinta yana kan hannatou. Wani lokaci irin wannan yanayin yana kasancewa takura a tare da ita,duk da kasancewarta mutum me tsananin jin girman da take dashi.......amma yanzun bataga dalilim taruwrasu ba dukka haka suna marabtarta. Inda kowa yayi zamansa zata nemeshi idan buqatar hakan ta taso. Wata dabi'a ce a cikin jininta,sam bataso bata kuma qaunar a dinga shiga al'amuranta muddin ba itace ta gayyatoka ba. Ita dinma tana da dabi'ar yin halin ko in kula da al'amuran wasu,koda ya shafeta ballantana bai shafeta ba. Hannatou ita ta kasance kamar wata idanu na me martaba a nam Niamey gidan da akhnan ke rayuwa......hadima ce itama da asalin kakanninta suka kasance bayi ne ga kakan akhnan sarki muhammad agg bin muhammad agg abba. Tana da wani matsayi daya sha banbam dana sauran dukka hadimai da bayi,don hatta iyayenta basu mutu a mazaunin bayi ba,sun samu 'yancin kansu tun zamanin sarki muhammad agg din. Tana iya yiwa akhnan gyara,tana iya nusasheta kan wasu abubuwan ta sigar shawara da hikima da dabaru da Allah ya hore mata a shekarunta da Allah ya bata. Akwai sabo tsakaninta da akhnan din a yawancin lokuta,duk da sabon bai hanata aiwatar da duk abinda take ganin yayi daidai da tsafinta da rayuwarta ba,koda kuwa a hangen hannatou hakan ba daidai bane. Tun tana da shekaru goma a duniya hannatou ke tare da ita,kebantacciyar hadimar da ta dauki nauyi da dawainiyar wahalarta tun kafin tasan kanta,wannan dalilin ya sanya da wasu abubuwan akhan din take sauraren hannatou din,ta kuma sake da ita har sama da yadda take sakewa dasu birra kuwa,duk da yadda suke 'yan kusa kusa da al'amuranta. Ajiyar zuciya ta saki me nauyi sanda ta zauna sosai saman gadon nata gana kuma sheqar daddara iskar da dakin nata ke bayarwa. Tana matuqar qaunar dakin qwarai da gaske,dakin yana da wani irin yanayi na musamman da kuma tsarin ginin da ya dace da zabin akhnan din. Ba dakin kawai ba,gidan gaba daya na musamman ne a wajenta,saboda yadda take samun sakewa sosai da kalar yanayin da tafi buqata a rayuwarta. Ba gidan bama,ita kanta Niamey na daya daga cikin garuruwan da take so sosai,saboda tana bata irin yanayi da nutsuwar da take buqata a yawancin lokuta fiye da agadez. "Mun dauka zaki kai zuwa wani satinne biftu" Hannatou dake maida luggage din akhnan inda ya kamata ace suna zaune ta fada,da sunan da banda hannatou din ba wani cikin hadimai dake kiranta dashi sai ahalinta kawai. "Na gama abinda ya kaini hannatou.........dama kawai rigima ce irin ta sultane" Murmushi hannatou ta saki kawai,ta sani indai biftu din ta fadi haka sultane din yayi wani da baiyi daidai da tsarinta ko abinda takeso ba kenan. "Ran sarki ya dade......kullum hangensa shine yadda biftu zata zama mutum ta musamman......" "Banda a nan hannatou.......na taba ganin inda aka tursasawa mace tayi aure bisa dole?" Ta fadi da alama maganar har yanzun bai qare ba a ranta. Abinda hannatou keyi ta bari,ta dawo gefan akhanan tana taimaka mata wajen fidda takalmin qafarta da take cirewa da qyar,tabbacin hidimta mata a komai nata da zatayi ya zame mata jiki.......bata iya yin komai da komai wa kanta a karan kanta kenan inaga hidimar da ba ta jikinta ba. "Koda yaushe sultane me gaskiya ne.......sultane me hangen nesa ne.....zai kuma ci gaba da kasancewa hakan har abada koda akan kanki ne biftu........a ganina da zaki bude zuciyarki ki fahimci maganganunsu da zaifi alkhairi da alfanu......aure cikar diya mace da qarin darajarta ne......." "Wacce daraja hannatou?......ina daraja wajen zama qarqashin wani bisa dokokinsa da umarninsa........ina daraja wajen rayuwa cikin mafarkin wani ba naka mafarkin na qashin kanka ba?" Tayi maganar tana waro manyan idanunta wane kamar waddda taga wani abun tsoro daban. Kai hannatou ta girgiza tana murmurshi,ba shakka sai yau ta gasgata akwai tarin tasirin quruciya akan akhanan ba 'yar kadan ba.......ta sani da dadewa cewa duk abinda yazo bakinta tana fadi muddin iya gaskiyarta kenan,sai a yau ta sake yadda da hakan. Ta manta su din suna rayuwa ne qarqashin umarnin wasu mafarkin wasu kuma rayuwar wasu?,amma hakan bai rage musu komai ba saima daraja da suka samu ta silar hakan da ingantacciya kuma amintacciyar rayuwa. Tana can tana laluben ta yadda zata fahimtar da akhanan din ta tsinceta har ta miqe tana fadin. "Zanyi sallar azahar.......bayan nan inaso na kwanta na huta........banaso a tasheni sai zuwa sanda na farka" "An gama zuciyar sarki zinariyarsa.........a huta lafiya" Ta fadi tana miqewa da takalman akhanan din,tayi musu mazauni sannan ta fice tana rufe mata qofar. Hankali kwance ta dauro alwala sannan ta fito,tana jinta a sake kamar dan prison din da ya samu 'yanci. Kayan jikinta ta sauya zuwa Palazzo pant da wata cross front blouse data fidda qirarta. Wani irin shape gareta da tasha jin aisa da Shehinaz na maganar muddin zata saka kayan da zasu lafe a jikinta ko yaya ne. Boobs dinta ne kawai basu fiya girma ba,don aisa tace inda sunfi haka girma tabbas fitinar sai tayi yawa Kuma. A dole a sannan ta saka akhanan din dariya,duk da ba'a cikin mode na dariyan take ba,don suna tsaka da fidda lissafin shekara ne na kamfani,abubuwan duka tana jin sun cabe mata. After dress ta dora saman kayan,tayi Rolling da babban mayafinta tayi sallah. Dogayen riguna ne daban da ita wanda aka ware mata don yin salla,a gida ko a office,don bata da wani hijabi guda daya da zatace ta mallaka. Taci bashin bacci jiya,don bata kwanta da wuri ba,wannan ya sanya tana kammala sallar ta zare dogon rigar da mayafin ta watsar a nan kamar yadda ta saba don tana da masu killace mata ta haye gadonta. Kusan dabi'arta ce haka,ba wani abu da takeyi bayan sallah daya wuce tashi daga gurin. Sau tari kafin takai haka suna sallah tare da sultane,tana mamakin yadda bayan sun gama sallar yakan dade saman dardumarsa kafin ya tashi,koda ta tambayeshi murmushi ya saki,ya kuma gaya mata alfanun hakan. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 12 "Akwai azkar masu yawa da akeso baya mutum ya kammala sallah ya yisu kafin yabar gurin......bugu da qari kuma zama a inda mutum ya idar da sallah ba tare daya tashi ba ko yayi magana,yana samun ribar nema masa gafara daga wajen mala'ikun Allah har sai ya tashi daga gurin,to kinga inda bawa zai dawwama a wajen zaiyita samun gafarar Allah ne ba yankewa,wannan ya sanya zakiga wasu mutanen sun lazumci zaman masallaci.....sallah bayan sallah". Kai kawai ya gyadawa sultane,ita sam irin mutanen nan ma basa burgeta,tana musu kallon mutanen da suka takura rayuwarsu ne kawai,bayan ba haka ubangiji yake ba,basai ka tsananta ko zurfafa akan komai,indai zaka kiyaye haram da halak shikenan. Da tanayi subhanallahi walhamdulillah wa la'ilaha illallahu wallahu akhbar kowanne talatin da uku......to amma daga baya da rayuwa ta miqa,abubuwa sukayi yawa saita watsar,sai lokaci bayan lokaci. Akwai malaminta da sultane ya dauko musamman don koyar da ita karatun addini,saidai sam rakiyar batayi nisa ba tace sam malamin baiyi mata ba. Ta kuma dora masa wata muguwar tsana da har takai kafin ya iso gidan zaa nemeta a rasa,ko zaiyi awa nawa kuma babu me sakin ganinta har sai ya tafi. Sam sam bata jin dadin karatunsa.......yana cikin mutanen da basu iya koyarwa ba sam sam,ta wani bangaren kuma a hankali ta fahimci mutum ne shi meson zuciya sosai,kamar irin mutanen nan da ake kira 'YAN CI DA ADDINI,ko ita yana iya roqo,duk da a sannan sultane yasa an tsaya masa da komai,albashi me kyau ci da sha na iyalinsa gaba daya. Baiyi karatun Boko ba ko kadan...... Hakanan karatun addinin nasa bai azashi daidai da yadda yazo daga asali da tushensa ba,asalin daya kasance salsala kuma tushiya ga dukka wani ilimi da wayewa da bature ko me jan kunne ke taqamar yana da ita.......wannan ya sanya duk wata wayewa sukayi hannun riga da ita,sai zallar gidadanci.......rashin wayewa da kuma qauyanci zalama da son abun duniya. Wannan shine abu na farko daya DASA mata wata irin MUMMUNAR AQIDA DA MUMMUNAN ZATO a ranta......muguwar tsana qiyayya da kuma qyama. Ko meye zakayi masa muddin akan abun duniya ne ba komai bane a wajensa,uwa uba ma sam jininta da nashi baizo daya ba.......tun daga wannan lokacin take wa duk wani mutum irinsa wani irin kallo......wani irin mummunan fassara da kuma nesanta kanta da duk abinda ya shafesu. Har tsakiyar kanta taji knocking din yana ratsata duk kuwa da nannauyan baccin da tayi nisa a cikin sa. A hankali ta bude idanunta tare da wani irin bacin rai daya sauko mata. Batasan wanne me gangancin bane yake tashinta,bayan kowa ya sani doka ce......ba'a tashinta muddin tana bacci har sai sanda ta tashi don kanta. Wannan dalilin yasa kowanne time na sallah take saka masa alarm muddin zata kwanta,don sallar na cikin abu qwaya dayan data yiwa riqo me kyau......bata kuma yarda ita ko lokacinta su kufce mata komai girma ko muhimmancin abinda takeyi. Hannu tasa ta dafe kanta jin ana ci gaba da knocking din kamar ba'a san dakinta ake qwanqwasawa ba. Ta miqe a fusace tana wantsalowa daga saman gadon,cikin ranta takejin ko waye wannan yau yake mata wannan gangancin ya kade a wajen ta. Mutum biyun data gani a tsaye a gabanta sun kaure da magana a tsakaninsu,wanda maganar da sukeyi ma ta sanya basuga ta bude qofar ba. Bataji hayaniyarsu ta ciki ba don qofar irin qofofinnan ne da ba zakaji hayaniya daga waje ba,hakanan daga cikin ma kaima ba za'a jika ba. Aisa da Shehinaz........sashenta.......'yan uwanta kuma aminanta. Idanunta da suka qara girma saboda bacci ta zuba musu,ganin bilhaqqi hira suke kaman wadanda suka shekara basuga juna ba tare da sun kula da fitowarta ba. Ta shiga uku.....ciwon kanta guda dayar ta dawo,wadda wani lokaci har tafi aisa daga mata hankali. Baqar buzuwar da kalar fatarta tasha bamban da tasu fatar ita da aisa,saidai akwai wani sirrantaccen kyau itama da take dashi qasan chocolate colour skin dinta. Shehinaz dince ta fara lura da an bude qofar "Elle a ouvert la Porte(ta bude qofar)" Ta fada tana fincikar hannun aisa. Matsawa gefe tayi tana basu hanya sanda suke wucewa ciki abinsu suna mita "Tu pionces comme un mort(kina bacci kamar gawa)" Still Shehinaz ta sake fadi tana yin ciki abinda. Goshinta ta dafe kawai tana ci gaba da jin hargaginsu sanda suka isa dakin. Wannan me shegen faransancin tasan ta kade a hannun ta itama,don ta tabbatar aisa ta gaya mata abinda tace data bata labarin abinda ya hadosu da Jamaal. Daidaita kanta tayi sannan ta juya tana komawa dakin. "Wai don Allah bakiji toc toc namu ba?". Scarf dinta kawai ta dauka dake ajiye saman dressing mirror ta daure sassalkan gashinta. "Biftuuuuuuu" Shehinaz ta sake qwala mata kiran da sai data dakata daga shiga toilet din ta waiwayo ta ware mata blue eyes dinta "Ban bude bane Shehinaz?......Fiche-moi la paix(ki qyaleni don Allah)" Ta qarasa fadi kaman zata saki kuka. Bata doguwar magana ko hayaniya me yawan idan ta tashi a barci,dukkansu sun sani haka yanayinta yake,amma yanzun gasu sun sakata a gaba zasu addabeta,kuma ta fahimci plan ne. Samu tayi ta wuce bandakin ta barsu a nan,a gurguje tayi tsarki ta daura alwala,tana mamakin baccin da tayi haka,har yayi nauyin da ko alarm dinta ma har yayi kuwwarsa ya gama bata ji ba,na qarshenne ma ta jishi kamar cikin mafarki,kuma ta miqa hannu ta kashe taci gaba da baccinta. Muddin ta gaji da yawa ko kuma ranta a bace yake to takanyi nauyin bacci,don haka ba kowanne guri take sakin jiki tayi bacci sosai ba. Har ta fito ta shimfida abun sallah Shehinaz da aisa basa jin kawunan juna. A nutse ta bada faralin sallarta,wanda tana dab da idarwa kira ya shigo wayar Shehinaz din ta dauka,abinda ya kawo ragin karadinsu cikin dakin. Zaune kawai tayi saman abun sallar itama,dakin sai ya zamana ba sautin kowa saina Shehinaz dake amsa waya can qasa qasa,don haka aisa ta jawo remote ta fara canza channel daga makekiyar tv din dake maqale a bango. Sannu a hankali takai channel din iman. Wani program akeyi da wani matashin malami da a kallo daya zaka fahimci yadda ilimin addini ya ratsatashi. Ajjiye remote din aisa tayi tana maida hankalinta kan tambayoyin da akeyi masa. A hankali maganganunsa suka fara shiga kunnen akhnan,saita daga kai ta dubeshi sannan ta tabe baki. "Zaki iya kashemin wannan tv din ko ki maidashi a bluetooth daidai kunneki?". Kai aisa ta dago ta zaro idanu waje tana kallon akhnan. Ta rasa wanne irin alaqa ke tsakaninta da duk wani matashi da zaiyi kamanceciya da malami ko me ilimi na addini kamar haka,karàtuttuka da lectures duka idan tana wani abun ka kunnashi a gabanta yana zame mata kamar takura ce. "Baki da Imani........télé dinne zan sakawa Casque audio?" Kafada kadan ta daga cikin basarwa. "Eh.....II semble que vous vouliez le regarder(naga kamar kinason kalla ne)". "C'est intéressant(yana burgeni)" Ta amsa mata kanta tsaye. Maganar ta fusgi hankalin akhanan,har ta waiwayo da sauri tana duban aisa ba tare data shirya ba. "Shi wa?" Ta qara tambayarta tana watsa mata manyan blue eyes dinta "Shi malamin" Aisa ta fada kanta tsaye tana duban idanun akhanan dake bayyana zallar mamaki. Shuru ya ratsa tsakaninsu a dakin,har hakan ya dauki hankalin Shehinaz dake waya,sannu a hankali akhnan ta motsa ganinta akan aisa sannan tace. "Kuma kina nufin abinda kika fada dinnan har zuciyarki?". " Yes......har qasan zuciyata" Aisa ta furta tana bata tabbaci. Wani abune ya tsargawa akhnan har qasan zuciyarta,kamar ba zata dauke ido daga kallon aisa ba,kafin daga bisani ta janye duban nata tana rasa kalmar da zatayi magana da aisa da ita. "Ki fahimci wani abu fa.......wani boyayyen sirri ne cikin soyayya da auren malami ko auren ma'abocin sanin ilimin addini........akwai wani alfanu da wani boyayyen sirri da sai wanda ya auresun kadai yake ganewa.......su na dabanne......." "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Kawai taji akhnan ta saki. Sosai mamakinta ya ninku sanda taji tana maimaitata ba tare data juyo kuma ta kalleta ba. Kalmar nada wani irin girma da nauyi a qirjin dukka musulmi,wannan ya sanya Shehinaz yanke wayar da takeyi ta dubesu tana rarraba ido a tsakaninsu adan rude. "Lafiya?,Que se passe-t-il?(me yake faruwa?". " Aisa zakiwa wannan tambayar,nikam tafi qarfina" Akhnan ta fada tana tsugunnawa ta kwashe abun sallarta tana zare kayan sallar jikinta. Harga Allah har zuciyarta takejin maganar aisa. Bata mata fata ko sha'awar auren irin mutanen nan sam sam,ba aisa kawai ba.....duk wada take qauna yake kuma tare da ita,don bata hangi komai a cikin hakan ba face wani gagarumin ci baya da koma baya,bataga kuma abinda za'a tsinta a cikin hakan ba. Tana jinta tana yiwa Shehinaz bayani da dukkan gaskiyarta,kawai saita koma ta zauna saman Beanbag chair ta zauna tana zurawa lausasan qafafunta socks saboda sanyin marbles din da takeji suna shigarta. A gefe daya tana ci gaba da jin maganganun aisa dake qara kare muradinta da kuma hujjojinta,saidai daga ita har Shehinaz ba wanda yace komai,batasan dalilin Shehinaz nayin shuru ba.......amma tata hujjar takaici ne da baqinciki kawai fal qasan ranta,sai kawai taja wayarta ta kira birra tace ta shigo mata sa fruit zata sha,ta maida jikinta cikin bean bag chair din ta kwantar abinta ba tare data sake tankawa kowa ba har birra ta shigo da nau'ikan fruit din da tasan akhnan din na ta'ammali dasu saman wani kyakkyawan tray. A yayyanke suke cikin wani irin yanayi da tsarin da zai baka sha'awa matuqa. Kusan dukka sun haddace wani tsari nata dama abinda tafiso tafi kuma muradi. "Za'a dora dîner........ko kina da buqatar a dora miki wani abun daban?" Kai ta girgiza a hankali tana karbar spoon da pork din hannunta dake nade cikin fararen papers. "Ku dafa iya cikinku......" Kai ta gyada,tunda taji ta fadi haka hakan yana nufin ba'a gida zataci abincin dare ba,ko kuma ba zataci abincin daren bama duka. Duka tana iya yiwuwa,wani lokaci tana fita French restaurant taci French cuisine,musamman irin taste da aroma nasu da tayi missing. Tayi zaman French na shekaru biyar,don haka da yawa wasu abubuwan nasu ya zauna mata,tana kuma wasu abubuwan irin nasu. "Kin fahimci dalilai na ko?" Aisa ta jefawa akhnan tambayar. Tsaida kankanar data dauko da pork tayi ta daga idanu tana dubanta. "Wa?" "Ke mana" Aisa ta fada tana dariya qasa qasa,da alama akwai manufa a dukka abinda tayin. "Bansan ma magana kikeyi ba ai bare na samu lokacin saurara,Ce que je sais,c'est....(abinda na sani shine),yaranki saisun tsine miki sunyi Allah wadai da uwarsu data rasa uban da zata zaba musu sai kidahumin uba" Baki aisa ta bude,yayin da Shehinaz ta miqe da wayarta a hannu kawai tayi qofa. "Biftu......Es-tu sain d'esprit?(kina cikin hankalinki kuwa).......kinsan su waye kikewa kallon kidahumai.......?" "Continuez(ci gaba)" Ta fadi tana miqewa tsam itama ta dauki farantin ta fita duk da batayi niyya ba,saidai ba abinda maganar aisa ke saka mata sai bacin rai. Idan taso jan musu aisa ta iyashi,idan taso jan magana ma haka,saidai ka sakar mata ko ka biye mata kuyita yi,abinda kuma ita sam bata iyaba kenan,wannan sai ita sa Shehinaz. Wani lokaci idan suka fara harji takeji kamar kanta zai dauki ciwo,bata iya dogon magana bata kuma iya bada haquri ba,saidai ta tattare 'yan kayanta kawai tabar musu gurin,idan sun qoshi don kansu sai su bari. "Dadina dake mugunta.......baki iya raba husuma ko gardama ba ko za'a yi kisa ko?" Shehinaz kan fadi tana jifanta da harara,hararar da yawancin lokutama batasan tanayi ba,don ba kasafai take daga kanta ko ta bata hankalinta ba. Wani lokacinne idan 'yan maganar suna kusa takance "Tunda ni na sakaku dole na tashi hankalina wajen hanaku" Daga wannan sai taja bakinta ta qara bamewa. Itakam duk duniya idan kanaso kaga nutsuwarta da bada dukka attention dinta kan abu to abinda ya shafi aikin kamfaninta da office dinta ne.....wannan kam zata iya kashe masa ko awa nawa ne......sallah kawai ke tashinta. "Ina da baqo gobe.......na kira ana na gaya mata......sannan na gayawa baba soulaimane shima" Shehinaz ta fada tana qoqarin saka wayarta a charge. "Allah ya kaimu.....zaki baro,Allez-vous quitte le bureau tôt(zaki bar office da wuri?)" Kai ta jinjina "C'est Exactement ce que je pense(haka nake tunani)" Ta amsa mata tana kulle wayar gami da nufar hanyar kitchen don ita din mutum ce meson girke girke. Zai wahala ayi wani girki bada ita ba,wannan ya sanya ta iya girke girke da yawa,aisa ke biye mata wani lokaci itama tana kwaikwayar wani abun,takance. "Bari mu dinga pratique......naga mazan yanzun sun baci don girki". Sau da dama tana gefe tana aikin office abinta. Itakam koyon girkin yana cikin abu na sahun qarshe da bata taba tunanoshi hasasoshi ko kawoshi cikin rayuwarta ba. Tana ganin meye hadinta da girki?,ba girki kadai ba,kitchen dinma in general bata da wata alaqa dashi. Ba zata iya tuna lokaci na qarshe data taba koda dora ruwan zafi da kanta ba balle ayi maganar girki. Duk wata hidima da zatayi ko zata taso mata tana da masuyi mata,so ko a hasashe.......ko a mafarki bata taba kawo girki cikin agendas na rayuwarta ba. ★★★ zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *234 9166221261* *Safiya musa abdullahi* *MY NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 13 ★★★Kamar kowane lokaci sanye take cikin wata lallausar atamfa da aka yiwa dinkin buba,irin dinkin daya sake batar da kamannin atamfar sosai,idan ka kalleta da kyau karon farko ba zaka dauka atamfa bace,zakayi tunanin wani yadi ne na musamman cikin yaduka masu daraja da tsada da takan sanya lokaci lokaci. Ranar tana daya daga cikin ranakun da me martaba sultane yake samu ya huta a cikinsu,musamman yau daya kwana da mura jikinsa sai ya zamana babu dadi. Musamman ta shirya masa riz kissé da soyayyar plaitain da wasu hadin vegetables na musamman. Ba wani abinci bane na daban a sunan da kuma idanu,saidai ya zama na musamman a dandano da kuma irin qamshin da yake bayarwa,qamshin kayan spices na musamman da ya sanya abincin morsa safiyya ya fita daban daga dukkan dandanon wani abinci a harshensa. A kashingide ta sameshi cikin wata lallausar shimfida dake da tsananin taushi. Yau din ya fito a buzunsa kuma ba'adazensa sak,don kuwa riga ce 'yar shara a jikinsa ta wata dakakkiyar shadda da kum dogon wando,sai rawanin dake kansa wanda yayi masa nadi na cikakkun buzaye. Shafukan qur'ani ne a hannunsa bugun warsh yake karantawa ciki ciki,amma shigowar safiyyan da kayan abincinta ya sakashi ajjiye qur'anin,ya kuma miqe ya zauna sosai yana murmushi. Safiyya kenan iya rigima yake fada qasan ranshi. Ba tun yau ba yasan wannan,gwanar iya tunkarar duk wani nau'in rigima ne idan taso........idan kaso kuma komai zai wuce kamar bai faru ba. "Marhaban lale" Ya fada yana miqa hannu zai karba mata kwandon. Janyewa tayi tana murmushi da accent dintan nan na yarensu tace. "Bazan baka aiki ba.....kaida kake cikin lalura?". Murmushi kawai yayi. Kaman ba shekaran jiya aka gama hatsaniya da ita ba,ta birkita masa lissafi ta kuma birkitawa kowa. Sosai ta zauna tana gaidashi cikin bashi girman da Allah ya bashin,ya amsa yana janta da tsokana,sai ta saki murmushi kawai ta jawo kwanukan abincin ta fara budewa. "Me nassamu ni muhammadu?" Sosai maganar tasa ta sakata sakin murmushi,ta jima da sanin cewa tabbas shi din yasha banbam da sarakuna sosai......ya musu wata irin tazara me girma,yana mu'amala da iyalinsa da irin salon da zai nuna maka bai dauki kansa kowa ba a wajensu. Zakasha mamaki ida kaje ka sameshi cikin fadarsa.....ko ya fita wani taro ya cika wajen da wannan kwarjinin nasa,zaka tsinewa kanka ba shine a yanzun zaune ba. "Tashi murmure na kawo maka". Tun bata gama zubawa ba yawunsa ya tsinke,ya sani bai taba yin matar da tasan martabar girki ba irin ta,tana da baiwa qarshe ta fannin iya abinci.......tana kuma bata lokutanta sosai wajen dafa masa abinci koda ba ko yaushe ba,girkinta a lokutanta yafi girkin hadimanta yawa. "Wannan toshiyar baki ne halan?" Ya fada sanda yayi lomar farko,dadin abincin yana ratsashi. Murmushi tayi tana sadda kanta qasa gami da murxa yatsunta kadan. "Har ka gano ni?" Ta fada muryarta qasa qasa. "Nafi kowa sanin halinki.......nafi kowa karantarki" Ya fada yana murmushi dadin abincin yana dibansa. Kai kawai ta jinjina,bata musa ba......bata kuma yi jayayya ba. Mutum ce da bata iya boye abinda yake ranta ko yake cinta,ko yaya ne abu yake damunta sai ka fahimta,kota gaya maka,ko ka gani a fuskarta,ko ka gani a aikace. Bayan rasa imraan,bata qara tunani ko hasashen samu miji kamarsa ba,sai gashi Allah yayi mata kyauta da sultane din......wanda koda cikin mafarki bata taba kawowa zata mallakeshi ba koda wasa kuwa. "Abincin cin hanci ne......cin hancin da na baka shine don ka tsaya ka fahimci zancan Allah da ma'aikinsa......zancan da yake da matuqar muhimmanci ba ga duniyarmu kadai ba......har lahirarmu" Tayi maganar a tausashe cikin qanqan da kai sanda ya kammala cin abincin yana miqe qafafunsa. Kallonta yakeyi sosai yana jin sautin muryarsa tana ratsashi,bazai ce ya maida gurbin safeena ba.......amma safiyya ta dabance.......daban take a zuciya da rayuwarsa. "Wanne zance ne haka me muhimmanci har haka?". "Batun amana ne.....magana akeyi akan amana" Ta fada yana sauke numfashinsa daga tambayarta da yayi. "Amana?" Ya tambayeta yana jin kalmar tayi masa nauyi. Kai ta jinjina tana dubansa. "Eh amana......amanar da safeena tabar maka......amanar da safeena tabar min.....wadda ni kam duk yadda naso ban isa na sauketa ba saida hadin kanka da goyon bayanka". Kai ya sake jinjinawa,zuwa yanzu hankalinsa yakai inda take nufa. Ganin maganar zatayi mata daidai da yadda take so ya kasance saita gyara zamanta sosai tana sake qanqan da kanta. "Nasani ka sani......manzan rahama da kansa yana cewa......namiji me kiwo ne a gidansa......kuma zaa tambayeshi gami da abinda aka bashi kiwon.....kiwonnan kuwa ya hada da mata da 'ya'ya.......Allah yana cewa......yaku wadanda kukayi imani ku tsare kawunanku da iyalinku daga wuta......wanda wannan wutar makamashinta sune mutane da duwatsu......safeena ta tafi tabar maka amanar biftu.....shin a ranar gobe kana da kowacce amsa da zaka bata akan khadeejah idan ta tambayeka game da ita ba tare da d'ar d'ar ko tunanin ka kuskuro ta wani fannin ba?" Ta qarashe maganar da tambaya. Tambayar data masa nauyi sosai,ta kuma tilasta masa yin shuru,idanunsa akanta har lokacin. Kanta ta girgiza sannan taci gaba da magana. "Musulunci ya bawa iyaye daman zabawa 'ya'yansu yammata mijin aure.....hakan daidai ne,saboda ya duba cewa qila hankulansu basu nuna ba bare su zabawa kansu mijin daya dace da rayuwarsu......akwai sakin hannu me yawa game da damar daka bawa biftu.......ba zata iya ba......ba abinda zatayi wataqila saici gaba da wulaqanta masu daraja.....wanda akwai tafkeken kuskure cikin hakan.....altaab shine na tara da taqi amsa a mazaunin mijin amre......kana lissafe?". Maganar tata ta ratsashi sosai. Don sam wannan lissafin bai taba zuwa kansa ba. "Baka tsoron wani ya cutar da ita ta wannan hanyar?.....ko bada sihiri ba qullaci idanu da baki dukka suna iya zamewa rayuwar bawa masifa". "A'uzubillahi min kulli ainin lammah......wamin kulli shaidanin hamma" Ya furta a nutse wanda ta tabbatar yana nemawa diyarsa tsari ne daga abinda ta fada. "Neman tsarinnan ranka ya dade ya kamata ya zama a aikace......ta hanyar taimakar diyarka ka zaba mata miji ma'abocin addini da zai saita rayuwarta" Sosai yake dubanta da maganarta ta qarshe yana fassara hakan cikin kwanyarsa. "Eh.........namiji me addini shine kadai wanda zai iya gyara rayuwar biftu.......namiji me cike da nutsuwa da hasken addini......shi kadai ne zai cike gibin da aka bar mata cikin rayuwarta.......shi kadai ne zai iya kula da ita......ya dinke kowacce kalar baraka dake tsakaninta da ibadunta da mahaliccinta dama mutanen da take rayuwa tare dasu.......namiji me addini ne kawai zai riqe hannunta daga duhu zuwa haske......shi kadai ne fitila cikin rayuwarta......akwai tarin gyare gyaren da shi kadai ne zai mata nuni dashi......muddin kana buqatar tsiron nagartattun jikoki da zasu iya riqe masarautar AGADEZ daga fita daga hannunka.....a nan kusa muddin kanaso kaci moriyar jikokinka.....idan hakan bata kasance ba kuwa zai zamana dukkan wata dama zata qarasa subucewa daha hannunka". Wasu irin dunqulallun maganganune da suka jima cikin zuciyarta da ruhinta......wasu irin dunqulallun maganganu masu tarin yawa da yau ta samu ta warwarewa sultane su......wata dama da taketa fama taci gaba da samunta har abada......damar da take sanyan ran da ita kadai zata iya tsaiwa gaban safeena ta gaya mata NA BAWA KHADEEJA GUDUNMAWA IYAKACIN QARFI DA IKONA. Maganganun da suka dauki tunaninsa suka maidasu saman saitin da yakejin ya kamata su kasance. "Na gode sosai safiyya......ina alfahari da samunki......saidai alqawari ne na yiwa kaina.....muddin raina ko yara million nawa na haifa bazan taba musu auren dole ba.....kowacce cikin yarana tana da damar farko......saidai idan ta gaza a damar farkon.....wala'alla a dama ta biyu ta rasa damarta" Dan murmushi ta saki,don iya wannan kadai daya fadi ya bata nutsuwa da tabbaci. "Bashi da alfanu.....saidai sau tari idan har an kaucewa son rai,ita kadai ce take zamewa iyaye damar fidda yaransu zuwa turbar tsira......na aminta da alqawarin daka daukarwa kanka.......na yarda dakai kuma kan zaka canza komai.........." Kai kawai yake jinjinawa,saita rage masa tsahon tunanin daya jefa kansa ta hanyar gyara zamanta sannan tace. "Dazun da safe munyi waya da hairaan......mun jima muna tattaunawa da ita.......daga qarshe dai ranka ya dade......raina da hankalina bai aminta da ci gaba da zaman yaran nan ba a qasar nan......mun yanke shawarar zasu dawo nan suci gaba da karatunsu......zan nema musu malamin da zai dinga koyar dasu qur'ani da litattafan addini......domin duk rayuwar da babu karatun addini a cikinta rudu ce da fagabniya zallah......ruhin da ba qur'ani a cikinsa Allah ya taimakeka fanko ne" . Kai yake jinjinawa yana sake aminta da hankali da nutsuwar morsa din. Tana da zafi da gaske ne tana da fada.......amma kusan komai tana yinsa ne bisa gaskiya da hangen nesa. "Hakan yayi.....amma ko acan din nasan hairaan ba zata qyalesu haka ba ba karatun addini". "Allah ya baka yawan rai ayimin afuwa.... Duk yadda zaa basu na addinin nan baikai na boko yawa ba.....har abada yaro yaro ne......akwai kuma quruciya dukkaninsu a jikinsu......suna manta shi ilimin addini tamkar dan jagora ko sandan jagora ce ga makaho......shike saita kowanne ruhi da gangar jiki.....shine yake saita ruhi rayuka da rayuwa gaba daya". "Allah yayi miki albarka.....dawa dawa zaa taho?". Ya tambaya yana murmushi,don shi kansa kawai yana yin kara ne don kada ya shiga rayuwar yaran nasa..... Amma yan tsananin kewar jikokin nasa "Dukkansu me martaba,falaak din......sai aafreen da aeeda,shi Aaroon nace su barshi can gurinta ya zauna da Anwar dan uwansa,kafin lokaci yakai suma na tattarosu". " Ma sha Allah.....Allah ya kula mana da rayuwar su " Ya fada yana jin dadin hakan har cikin ransa. Duk da cewa falaak ce kawai jininsa.......amma yana jin hairaan a matsayin diyarsa halak malak........don daga jikin safiyya ta fito.....'ya'yan safiyya kuwa jinin safeena yana jin nasa ne. Idan ahalin suka hadu......yana manta cewa bashi da wani magaji tsayayye guda daya......yana manta cewa a yanzun ida ya fadi ya mutu sarautar qasar AGADEZ tana iya barin cikin gidansu ta fada zuwa hannun yaran gidan baffanninsa.....yasan komai na Allah ne.....muddin kuma akwai yiwuwar zaman sarautar hannunsu ba wanda ya isa ya karba,ballantana ma shi bai dauki gadon da wani zafi ba.... Don ko a baya zamanin kakanninsu ta taba barin hannun kakansa sai daga baya ta dawo musu. "Ranka ya dade.....bawai zakayi sabbin amare ba fa kuma a juya mana baya" Ta fada cikin sigar tsokanar data sakashi murmusawa har kyakkyawar wushiryarsa ta fito. ★★★★ Qarfe shida da rabi na yammacin ranar motar qirar Lamborghini ta ajiyeta a sashen ajiyar motoci na musamman dake gidan. Bude murfin motar akayi,daga gaba wani kakkauran matashi dake da komai baqi ya fito yana bude seat din baya. Iska ta furzar daga bakinta tana jefo qafafunta waje.......gaba daya jikinta yayi laushi saboda dadewar da tayi a zaune a office. Yau din harta gota lokacin tashinta saboda alwashin da taci tabbas sati me zuwa sabbin design na kamfaninsu zai fara zaga kasuwannin duniya. Duk da a jigace take,amma hakan bai hana bayyanuwar kwantaccen kyan da take dashi ba. Jikinta yana busa lallausan qamshin nan nata a kowanne motsi da zatayi,iska kuma na dada zaqulo qamshin nata sanda take kada tattausar lafayar data nade jikinta da ita,lafayar data yafata iyakar kafada,kanta zaune das da daurin dankwalin wani veil baqi me taushi daya zauna mata kamar hula. "Birra" Ta kira sunanta a gajiye..... Gajiyar data sake zame mata ado,don sai suka qara adadin yauqin halitta da yangar data zame mata ta asalin halittarta. Sign kawai tayi mata na ta karbi tarkacen office dinta dake hannun saaleem ta fara takawa zuwa gaba tana furta. "Wash Allah na". Gami da yarfar da hannu. Taku goma kacal tayi idanunta suka sauka kan Shehinaz ita da baqonta dake zaune suna facing juna..... Da alama magana ne sukayi me matuqar muhimmancin da har basa sanin meke faruwa daura dasu. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *MY NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 14 Idanu akhnan ta fiddo tana kuma rage dan saurin data aro daaa don isa ciki ta watsar da gajiyarta. Mamaki da tsoro suna cikata tana kuma sake ware idanunta akan baqon Shehinaz din,wanda bata sani ba,kaifin idanunta ne suka sanya yaji kallon a jikinsa ya maido dubansa sashen da take?,abinda ya dauko hankalin Shehinaz kenan itama ta maido dubanta inda taga yana kalla. Hannu ta dagawa akhnan cikin sakin murmushi,tashin farko taji ba zata iya maida mata koda da daga hannun ba bare murmushi ballantana akai ga takawarta zuwa inda suke,sai kawai ta dauke kai ta maida hankalinta zuwa hanyar da zata sadata da ainihin gidan zuciyarta na wani irin bugawa,bugawar da batasan meye dalilinta ba.....bacin rai ne?,ko kuma mamaki ne?,ba zata iya tantancewa ba. Da kallo dukkansu sukabi bayanta har ta bacewa ganinsu,sai Shehinaz ta dauke dubanta ta mayar kan Jamaal tana maye mamakin dake saman fuskarta da murmushi. Duk yadda taso wucewa daki kamar yadda ta tsara kafin ta iso gidan amma sai ta yada zango a parlor,abinda kusan ya bawa duka hadimanta mamaki. Saboda wani baqon abune da bata saba yinsa ba. Lokuta da dama ma idan ta dawo ta wuce ciki ba lallai bane ka sake ganinta ba sai washegari. Hannatou keda hidima da ita tana kai kawon bata abunsha da tasan takan sha idan ta dawo gidan. Buhaina na qoqarin tattare kayan office din data cire a nan,takalminta laffayarta dan kwalinta da jewelry dinta duka data zare. Ta saba komai tana ajjiyeshi ne a inda yayi mata,akwai masu kula da komai din su tattalashi. Xasu kwashe jewelry dinta a gogeshi kowanne a maidashi cikin box dinsa. A sake goge takalmanta ayi musu feshi a maidasu cikin qawatacciyar ma'ajiyar takalman dake cikin dressing room dinta. Wannan ya sanya komai nata idan ka kalla zakace ba'a sakashi ko ba'a taba sakashi ba,don hatta da qasan takalmanta babu wani datti da zai alamta maka haka. Tana da mugun qyanqyami.......sai Allah ya hadata da hadimai na amana dake iyayi mata komai kamar ko fiye ma da yadda takeso. Ganin hankalinta ba'a gurin yake ba sai Hannatou ta janye hirar da take dan sako mata. Agogo ta kalla dake bango don tuni ta cire na hannunta an wuce mata dashi. Ta soma gajiya da zaman jiran shigowar Shehinaz,kuma alamu sun nuna bata da niyya ko yunqurin shigowa a yanzu,dole ta miqe don wucewa ciki ranta na sake sosuwa. Taso qwarai Shehinaz ta shigo da zafi zafinta kafin ta sauya ra'ayin yi mata magana. Dab da zata wuce hanyar da zata sadaka da dakunan baccinsu taji shigowar aisa. Ta biya ta wani guri ne bayan sun tashi daga office,don haka yau tafiyar tasu daban daban take. "Kinga Shehinaz?" Ta tambayeta da muryarta a sanyaye. Bude idanu aisa tayi tana kallonta. "Eh na ganta ita da jamaal.......so masha Allah wallahi......Il a une maturité étonnante,II a une apparence trés religieuse(akwai alamun kamala sosai tare dashi,da alamun addini sosai tare dashi)" Ta fada kanta tsaye fuskarta na gasgata abinda ta fada har cikin zuciyarta yake fitowa. Baki da idanu kawai akhnan ta saki tana duban aisa,maqogoranta taji kamar ya bushe duk da bata jima da shan ruwa ba.......ta tattaro ragowar yawun bakinta ta hadiya sannan tace. "Aisa.....Êtes-vouse conscient de ce que vous dites(kina sane da abinda kike fada?)......kina tunanin mace irin Shehinaz ta dace da kidahuman mazan da babu wayewa a tare dasu?" "Qidahumai?" Aisa na maimaita kalmar cike da mamaki. "Biftu?.....wai me kika dauki ma'anar KIDAHUMIN NAMIJI?.....Namijin da baiyi karatun boko ba?......namijin da ilimin arabiyya kawai yake dashi?,shine kidahumi?.....kinsan kura kuren dake cikin wannan tunanika naki guda biyu?". "Ehnnnn........ki gayamin,Vouse lui lavez le cerveau(ke kike wanke mata tunani).......wannan mummunar hanya ce......hanya ce mara bullewa.......a ajin da darajar rayuwarta?........namiji me wannan suffar II n'était pas qualifié(bai cancanci) ya zama mijinta ba.......ba wani guri da mataki na rayuwa da zai iya tsaya miki........ba wani abu me muhimmanci da zai iya tunkararsa saidai ya tsaya a bayanki ki zame masa garkuwa.......banason irin wannan namijin......koda yaushe nafison NAMIJI ZAKI NAMIJI GARKUWA.......wayewarsa da iliminsa basu isa su tsaya a kowanne mataki da me ilimin boko zai tsaya ba.......mu gaya ma kanmu gaskiya kuma itama ki gaya mata gaskiya...." Ta qarashe maganan cikin fada da bacin ran da aisa ta jima bata ga ta yishi ba,sai kuma tayi gaba fuuuu da dan guntun saurinta ta wuce dakinta har aisa na jiyo qarar rufe qofar duk da qofofine da sam saika qaraci zamanka dasu bakaji qarar koda motsinsu ba. "Mon dieu du ciel(oh Allah na)" Aisa ta fada tana komawa ta zauna saman kujerar dake daura da ita. Ba zafi abun yayi mata ba......mamakin dauka zafin da akhnan din tayi ne yake daure mata kai. Tabbas a dukka su ukun suna iya shawara akan rayuwar daya su tsaida matsaya ko si zartar. Tun asali tasan burace buracen akhnan akan iri mijin da ya cancanci ta aureshi masu yawan gaske ne.......tun asali tasan akhnan din burinta babba a wajen namiji ya zama me cikakkiyar wayewa.......me zuzzurfan matakin karatu a duniya gaba daya.......namiji me zarra sosai......tsayayye jarumi maras tsoro ko shakka......bata da burin namiji me ilimin addini muddin yana da ilimin da zai kiyaye ibadarsa daidai........abu na qarshe data tsana tafi kuma raina ajawalinsa shine.......namijin da zaiyu karatun arabiyya. Takan fadi wani lokaci idan magana ta tashi. "Banga hikima ba......banga basira da wayo a karanta arabic ba.......a matsayinka na namiji da aka sani da zallar gwagwarmaya.......ina wani gwagwarmaya a karatun da iyakacinsa ka zama malami me koyarwa ko karantarwa?. A sannan zata iya cewa bata fiya ganin aibu ko rashin dabara a maganganun akhnan nan ba.......amma sannu a hankali da girma ya ratsasu.......rayuwa ta rarrabasu zuwa wasu qasashe......cikin jinsina da yare sai dukka wannan tunanin yabar jikinsu.....Musamman su din da karatu ya cilla aisa Egypt yakai Shehinaz madeena.........akhnan tata qaddarar ta kaita French. Kusan kowanne ya dawo ne da sabon tunani......sabuwar rayuwa da sabbin mutane cikin rayuwar tashi. Tsaye kawai tayi gaban babban madubin dake toilet dinta tana duban kanta da kanta. Iska take zuqa tana fesarwa tanason saisaita yanayinta,tsahon wasu mintuna zuciyarta ta fara magana da ita. "Ki nutsu akhnan......ki nutsu.......baki isa ki sauya qaddarar kowa ba.......baki isa ki tsarawa su aisa qaddararsu ba.......taki qaddarar ce kadai a hannunki......kina iya lanqwasata ta sigar da kikaga dama(a nata tunanin kenan)......karki bata wannan relation Amitié din(dangantaka da qawance),damuwa da damuwar wani ba dabi'arki bace.....ki concentration akan abinda yake gabanki". "Mais(amma) Shehinaz ce fa?" Ta fadi a fili da siririyar muryarta tana jin abun yana tsaye mata a wuya,tasan ta damu ne kawai saboda Shehinaz dince.......su din kamar wani sashe ne na tata rayuwar. "Idan Shehinaz ce zuciya da tunaninku ba daya bane......dole a samu banbanci cikin rayuwarku" Wani sashe na zuciyarta ya sake tunasar da ita. Dole ta tattare komai tayi wani watsin tsiya dashi,duk da tana ji abun yana ci mata zuciya,tayi wanka ta fito har sannan bata sake jin motsin kowa ba,sai ta zauna a nutse ta shirya cikin wani budadden wando da blouse data lafe ta fidda shape din jikinta. Sanda Shehinaz ta shigo aisa ta saukewa complain din abinda akhnan din tayi mata,ta diba da zummar binta daki ta gaya mata dalilin mata hakan,don bata taba ganin jamaal ido da ido ba hakan ba yana nufin baqo bane ko bare. Riqota aisa tayi,don tasan rigimarsu bata qarewa. Akhnan shariya......Shehinaz mita da gaza yin shuru akan komai indai ya shafesu. "Jamaal bai yiwa akhnan ba.....saboda II semble trés religieux(yayi zubin masu addini)......har yanzu wannan tsohon tunanin yana tare da ita......mais(amma) idan kin yarda dani.....wannan lokacin kiyi mata irin abinda takeyi mana?" Aisa ta shawarci shehinaz,dan fidda ido shehinaz tayi tunda aisa ta fara maganar "Me kenan?" "Ki koyi shariya da basarwa.....karkiyi qorafi akan abinda tayi,Arrête de te plaindre d'elle(ki daina qorafi a kanta)indai akan Jamaal ne,Laisse-la vivre comme elle veut(ki barta tayi rayuwarta yadda takeso)yadda kuma ta tsara......kin fahimta?". A nutse shehinaz ta gyada kanta,ta fahimci abinda aisa ke fadi,wanda dama wasu lokutan idan ta cakude a tsakaninsu aisa din kadai tunaninta ke zama a jikinta ta ajiye mafita guda daya. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 15 *_ETHOPIA🇪🇹_* *_oromia region_* *_jimma_* K'abilar oromo daya daga cikin manyan qabilu ne da qasar Ethiopia ke dasu. Qabila ce data kasance ta musamman kuma ta biyu da yarenta yafi yawa a qasar Ethiopia din(afaan oromo),idan ka cire yaren Amharic yaren oromo shine na biyu da sukafi yawa cikin qasar Ethiopia din. Qabila ce da take da mawadata sosai,suna da qarfin arziqin,hakanan mafi akasarin al'adunsu suna nuna irin qarfin arziqin da suke dashi. Al'adun yaren oromo na dabanne,wasu irin al'adu na musamman girmama manya.....girmama yanayi gaskiya dayin adalci kyautata mu'amala tsakaninka da jama'a. Yanki na musamman suke dashi......da yawansu kuma sunfi yawa a jimma......wani babban gari dake dauke da wani irin yanayi(weather)me matuqar kyau dadi da kuma nutsuwa. Saidai hakan bai hanasu rayuwa cikin garuruwa da dama a qasar Ethiopia din ba.....kamar addis ababa capital na Ethiopia din da sauran garuruwa. Duk da kyau irin na al'ummae Ethiopia,amma qabilar oromo kyansu na dabanne. Wata irin launin fata garesu......da wani irin hanci da launin baki(lips) da yake sake bambanta da kowacce qabila cikin qasar ta habasha. *_irreechaa festival day_* *ABA JIFAR PALACE (Aba jifar mosque national mosque jimma)* Ba abinda ke fita daga ilahirin manyan sifikun dake da dogon zangon cimma kunnuwan al'umma na nesa da kusa.....saboda ingancinsu da yadda aka zamanantar dasu face daddan sautin karatun al_qur'ani me girma da qira'ar fitaccen makarancin alqur'anin nan dan asalin qasar habasha Ethiopia wato sheik afif muhammad taj. Sak da sak muryar ke fita da wani irin kwantaccen karatu da muryar dake qara nutsuwa cikin zukatan masallatan dama wadanda ke nesa da masallacin ba sallar suke bi ba. Wata muryar da ta zame wa al'ummar yankin ta daban kuma ta musamman.......duk da cewa salon karatun sheik afif taj ne.......amma kuma sautin muryar ba tashi bace sam sam. Akwai wani irin taushi da amo daya sake banbanta muryar data sheik afif taj. Duk da ta kasance yau din ranar juma'a ce.......amma cikar masallacin ta zama ta daban da kowanne lokaci saboda dalilai guda biyu. Dalili na farko yau din tazo musu a watan October ne......daidai da ranar da suke gabatar da bikin al'ada na irreechaa......biki ne ko ace festival da ya jima cikin qabila da yaren oromo ana gabatar dashi shekaru masu yawan gaske.....bikine da kafin musulunci ya mamayi qasar sukeyinsa don godewa abun bautarsu a shekaru daruruwa da suka shude,saidai bayan zuwan musulunci tun daga zamanin king Solomon da queen sheeba sai aka musuluntar dashi ya zamana daidai da tsarin da bai sabawa addini ba. Abun yaci gaba da kasancewa a haka har kawo yanzu da moti(sarki a yaren oromo)abba jifar abba yake kan tashi sarautar. Sarautar da a wasu fuskokin iya tsari tafi da mulki da kuma shigo da zallar wayewa a cikinta yaso yayi kamaceceniya da tsarin sultane muhammas hammud. Ya maida tsarin ya sakeyin daidai da yadda zai dace da addini. Festival din ya sanyashi ya zamana ranar ciyarwa ga marasa qarfin da dukka ya kasance daga yaren oromo dama yankin oromo gaba daya,ba iya jimma kadai ba. Ranar ya sake maidata ta zama ranar kyauta sadaka da miqa kayan abinci wa mabuqata marayu da marasa qarfi. Abun zuwa yanzu yayi girma da fadadar da bawai yankin oromo kadai ba......ana fidda abinci daga taskarsa da kuma masarautarsa a irin wannan rana da yayi yawan da ake fita dasu wasu garuruwan dake cikin qasar habasha gaba daya. Bayan kammala taron akwai zaman addu'a da saukar qur'ani da akeyi na musamman don sake samun wanzuwar zaman lafiya da yauqaqar arziqi da albarkar rayuwa ga kowa. Saidai wannan sashen,an qirqireshi ne qarqashin jagorancin d'ansa *Prinsii(yarima)SHEIK MUHAMMAD HAISAM ABBA JIFAR*. Shi yake kula da wannan sashen,shine kuma yake dauke da nauyinsa da dukka iyawarsa. Jajirtaccen d'a guda daya daya zamewa mooti abba jifar daya tamkar da dubu. Duk da bashi daya ya haifa din ba........amma ya zame masa na daban da samun irinsa ba nan kusa ba. Bashi kadai ba.......hatta da masarautar oromo dama yankin gaba daya sun shaida da hakan,wannan ya sanya ko a yau cikar masallacin SHEIK HAISAM na daga cikin dalilin sabbaba shi. Yariman da kaf tarihin yankin oromo ba'a taba haifar irinsa ba........yana da wasu irin personality daya jawo masa farinjinin da yake bawa mahaifiyarsa tsoro.......farinjinin daya sanya a dole ta tsaya tsaiwar daka da dukka qafafunta wajen nema masa kariya ta kowacce fuska,ta kuma kowacce halastacciyar hanya. Cikin nutsuwa da kamala ya sallame sallar,kafin sauran daruruwan mutanen dake binsa jam'i a babban masallacin suma su sallame,ciki kuwa harda mahaifinsa mooti abba jifar. Shuru masallacin ya dauka na wasu mintuna,sanda yake sadda kansa qasa yana karanta. "Astagfirullah astagfirullah astagfirullah,Allahumma antassalam,wa minkassalam,tabarakta ya zaljalali walikram,la'ilaha illallah,wahdahu la sharikalahu,lahul mulk wa lahul hamd wa huwa ala kulli shai'een qadir,Allahumma la mani'a lima a'a daita.....wala mu'udiya lima mana'ata wala yanfa'u zaljaddi minkaljadd". Can qasan ranshi,ya dora da gajerun azkar da akanyi bayan sallamewa daga sallah,sannan ya motsa cikin cikakkiyar nutsuwarsa yana fuskantar al'ummar dake bayansa cikin sahu. Dukkaninsu sa'annine na mahaifinsa sarki abba jifar dama wadanda suka girmeshi,idan ka cire mutum biyun da suka kasance sa'anninsa ne wato omari da taarik. Kaman yadda musulunci ya tanada haka ya miqa musu hannu sukayi musabaha cikin nutsuwa,wanda mahaifinsa sarki abba jifar ya zamana na qarshe da suka gaisa din. Murmushi ke sauka a fuskar moorti abba jifar.....murmushin farinciki,murmushin nasarar da Allah ya bashi na mallakar haisam a mazaunin d'iyan cikinshi,d'iyan nasa da baisan adadin mutanen dake buri da fatan inama ace su suka samu d'a irin nashi. Kyawawan kewayayyun idanunsa dake da wasu irin zara zaran eye lashes da kuma kwantacciyar girarsa data kusa hadewa da juna da tudun karan hancinsa da shatinsa ya bayyana kawai kake iya gani saboda wani salon nadin rawani da ya yiwa kansa ya lullube har hancinsa,amma hakan bazai hanaka fahimtar martanin murmushin daya maidawa mahaifinsa ba. Gaisuwar tasu tazo qarshe saboda motsawar dogarawansa,abinda ya sanyashi miqewa don shima ya shiga tawagar ayarin rakiyar mahaifinsa ba tare da damuwa da tashi tawagar dake jiransa ba. Yana daga gefan mahaifinnasa sanda suke takawa tare cikin zagayewar hadimansa. Cikin nutsuwarsa da dattijankarsa da ilimin addini ya yiwa ado yake takawa yana riqe da kaykkyawar baqar sandarsa me sulbi. Bai dakata ba har sai da suka qarasa bakin qaramar motar da yakan koma gida a cikinta a duk qarshen biki irin wannan. Motace qarama me wani irin launi da sarakunan qasar England sukafi amfani da irinta tun tale tale. Sai daya tabbatar da zamansa a motar,ya matsa da kansa ya gyara masa alkyabbar data kasance wani tambari na musamman na sarautarsu ya maida qaramar murfin ya rufe sannan ya rusuna cikin girmama da muryar da shi kadai zai iya ji yace "Keessummaa sana nan tuffadha(zan sallami baqi)" Kai mooti abba ya gyada cikin salo na sarauta,ya daga hannunsa ga haisam sannan motocin suka fara motsawa suna ficewa daga fargajiyar masallacin,wanda tazara kadance tsakaninsa da ainihin fadar mooti abba jifar din. Idanunshi akan motocin kamar meson tabbatar da lafiyar mahaifinnasa,sannan a nutse ya sanya yatsarsa yana jan rawanin dake fuskarsa daidai karan hancinsa yana sake rufeshi. "Fuula kee dhoksuu filatta(me yasa kafi zabar rufe fuskarka?)" Yaji an fadi daga bayansa,abinda ya sanyashi waiwayawa a nutse duk da ya fahimci muryar waye. Boyayyen murmushin nan nasa yayi cikin mayanin fuskarsa yana duban omari. Yasan ya sake maimaita maganar kawai don yayi tsokana.......ya kuma samu nasarar tuna masa da abinda shaf ya mance dashi. "Omari.......ba zaka daina ba ko?" "Ka gayamin ta yaya zan daina?,bayan nima naga abinda ta gani din?". Wani miskilin murmushin ya kuma saki wanda ba zaka samu nasarar ganinsa ba saboda rufaffiyar fuskarsa,ya kada kansa a hankali. "Kana yi kaman bakasan komai akan muhammad haisam ba....." "Idan nace nasan komai din kamar zai zamana na yiwa kaina qarya ne" Ya amsa masa yana bin bayansa sanda yake komawa zuwa babbar qofar masallacin don kaucewa idanu da kallon jama'ar dake wucewa nesa kadan dasu,don tunda har baibar masallacin ba masu tsaronsa yasan ba lallai subar kowa ya sake shiga ba banda na ciki da suka samu yin sallah a cikin wasunsu suma suke haramar fita. Yana tube rufaffun takalmansa da bayansu ya zamana budadde muryar tayi sallama daga gefansa. A nutse ya daga kai yana amsa masa. Salawi ne......wanda ya kasance me hidimta masa ta fannin kula da abubuwan hawansa......dokunansa da motocinsa. "Obbo(yallabai),a matso maka da farda(doki) ne?" Kai ya girgiza a nutse,so samu ma ya zauna cikin masallacin kafin ya wuce cikin gidan,to amma hakan yasan bazai samu ba.....don tabbas yasan anna tana can tana dakon shigowarsa......kome dare kuma bazata je ta kwanta ba sai ya shigo din. "A wuce dashi gida......zan shigo cikin gidan yanzunnan.......zamu tako da qafa". Ya qarashe maganar yana sauke idanunsa akan taarik dake shigowa,da alama shima akwai baqin daya sallama. Jijina kai salawi yayi yana juyawa yana barin gurin,tare da jinjina irin jarumtar uban gidan nasa,da cikakkiyar lafiyar da Allah ya hore masa. Wuni guda yau a tsaye suka yita,saboda tarbar baqin da bai zauna ba.....dashi aka dinga karbar baqin me martaba da sukazo taron har sai daya tabbatar anyi komai yadda zai dace da muradin mooti din......amma duk da haka yakejin zai qarasa gida a qafa ta hanyar kebantacciyar hanyar da zata sadaka da cikin gidan tun daga masallacin,wadda keda tsahon kilometers da kuma jami'an tsaron dake aiki a cikinta duk da ba kasafai ahalin gidan ke amfani da hanyar ba. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 16 Cike da mutuntawa ya qarasa cikin baqin da yawansu suka kasance abokansa ne.... Abokai kuma irin wanda suka hadu da juna ta hanyar Neman ilimi. Kallo daya zaka yiwa kowa a cikinsu ka karanci yadda ilimi yayi musu ado da wata irin nutsuwa ta musamman. Duk da kowa a cikinsu matashine da jini ke guda na a jikinsa yadda ya kamata......da yawansu matasa ne da suka fito daga gidajen sarauta da gidajen mulki......irin mulki da sarautar da suka mallakawa kowa jin dadi dukiya me yawa da wani irin kwarjini na musamman.......saidai wannan nutsuwar......wannan kamalar da wannan haibar da ilimin addini da qur'ani ke saukarwa kowanne ruhi dake da abota dashi ta mamaye kowannensu. Hatta da yadda lafuzansu na magana da yadda suke tsokana da raha a junansu ta tsaftatacciyar hanya kadai abun burgewa na. Kusan matasa irinsu da suka hada baiwa irin tasu,kyau.....mulki......sarauta,ilimin addini dana zamani......mafi yawa daga cikinsu lokacine nacin duniyarsu da tsinke ta hanyoyi daban daban,sharholiya da sauran abubuwan da suka saba da addini da al'adunsu. Kusan hirar tasu ta tuna baya ce.......don a cikinsu akwai wadanda aka jima ba'a hadu da juna ba,yau irreechaa day ta hadasu. Zolayar juna,tuna wasu abubuwa masu muhimmanci,abubuwa masu dadi da rashin dadin suketa yi wanda ya faru cikin makarantun da sukayi tare. Wahala da irin qalubalen da suka fata wajen haddar qur'anin da sukayi a shekarun qananun shekarunsu. "Har yanzu ina mamakin yadda muke kwamciya da dare baka kammala haddarka.......amma da safen saika tashi ka haddace karatun gaba daya harda qari akan qa'idar daya kamata a tsaya?". Siririn murmushi ya saki yana lumshe kyawawan idanunsa dake da wani irin shape da yafi almond shafe tsaho kadan. "Wannan baya baccin dare me yawa tun asalinsa.......amma nima ina da ayar tambaya a kansa wallahi.......inajin anya mooti bai bashi wasu sirrika ba irin na masarauta?". Dariyar dake cike da hankali suka saki,ya bisu da murmushi yana aza hannunsa gadon bayan wanda yayi maganar. Cikin sautin nan nasa da yasha banbam dana maza da yawa yace "Indai ina da sirrika na sarauta.......lallai ba shakka kai din bappi ya baka sirrikan mulki.......shi yasa kujerar ka da gadonka har muka kammala ba wanda ke kwanciya akai" Dariyar suka sakeyi,yana tuna musu da rigima irin ta mutallab. Yafi kowa rigima a cikinsu,sannan yafi kowa bata musu daki a wancan lokacin,to amma duk randa ya taqarqare yayi gyaran dakin tofa kowa ma ya shiga uku a wajensa,basu da sukuni basu da sakat. Wani irin team garesu a sannan me abun mamaki,ba wani a cikinsu da ubansa ba wani bane cikin qasar ta Ethiopia da maqwabtanta.......'ya'yan gata ne iya gata.......saidai gatan da yasha banbam da sauran gara gata,saboda wata irin tarbiyya da ilimin addini daya ratsa ruhin kowannensu,ya maidashi mutum me wata irin nagarta ta daban. "Banda dare yayi lokaci ya soma ja.......da mun taba musaffa koda ta izu daya ce......don bana tunanin nan kusa akwai wani lokaci da zai sake hadamu kamar haka......duk kowa a cikinku yaqi fidda mata yayi aure bare mu saka ran haduwa a kusa kaman haka" Daya daga cikinsu da suke kira da naseeb wanda dan asalin Egypt ne ya fada yana duba agogon hannunsa sannan ya sauke dubansa akan haisam. Shi din mutum ne me asalin fahimta da daukan haske akan magana ko motsin mutum.........hakan yake tun asalin halittarsa.......wannan ya bada gudunmawa sosai kan aikinsa na yanzu da yakeyi personally ba tare da kowa yasan wayeshi din ba. Yanayin yadda naseeb yayi maganar yasan me yake nufi,ina ya dosa. A cikinsu shidan naseeb yayi aure bada jimawa ba.......mutallab......khadeem.....maleek......amjaad......dukka suna da tsayayya.......shine har yanzu da babu koda wannan tsarin a gabansa,sau tari koda conference call sukeyi a tsakaninsu mutallab din kan tsokaneshi da cewa. "Don Allah ku nema masa tsayayya wannan.......wannan an rasa me tsaya masa". Omari ne kanyu murmushi......saboda shi daya ne yafi kowa a cikinsu sanin wayeshi.......yafisu saninsu rufaffen sirri me girma dake cikin rayuwarsa. Cikin qasa da mintuna talatin tawagarsu ta soma fita daga masallacin zuwa inda kowannensu abun hawansa da guards dinsa ke jiransa. Cikin wannan hirar da barkwancin gami da qaunar junansu,kamar ba zasu rabu ba haisam din daya kasance me masaukin baqi ya takawa kowa zuwa bakin motarsa cikin musabahar bankwana suka rabu. Ya rage dagashi sai omari da suke takawa a nutse zuwa sirrantacciyar hanyar da yakejin kamar nan ne kawai yafi dacewa suyi magana da omari,bayan masu tsaron qofar sun bude masa cikin rusunawa bayan ya wuce suka maidata suka rufe. "Omari......" Ya kira sunansa da tsinkakkiyar muryar nan tasa dake da wani irin amo......amon da hatta maza 'yan uwansa tana musu dadi ballantana diya mace. "Wani lokacin sai na dinga jin kamar wannan matsayin......wannan girman da ake bamu kaman yana neman wuce gona da iri.......kamar akwai sabawa mahalicci a cikinsa" Ya fada calmly kyawawan idanunsan nan dake da wani irin haske suna motsawa wajen rufe kansu da budesu a lokaci guda yana duban tsahon hanyar da suke takawa cikin nutsuwa. Murmushi omari ya saki......shi dinma daga gidan sarauta ya fito,da akwai banbancin yare tsakaninsa da haisam.....shi din yaren amheric ne......amma yanayin aikinsu ya sanya shida haisam din sukejin yaruka masu tarin yawa,harda yaren da ba na qasarsu bama,ciki kuwa harda yaren turanci bayan na larabci daya zame musu kamar yarensu na haihuwa. Sun iya hausa kasancewarta cikin yare mafiya girma da fadada cikin yarukan yankin africa,hakanan sun iya French......yarukan da suke cikin qasarsu kuwa kusan kowannensu saida suka iya shi,a qalla idan aka lissafa yare kusan goma suke ji,saidai ba kowa ne yasan da wannan ba. A yadda omari yake kallon komai,duk wani motsi na gidan sarautar abba jifar yana cike ne da zallar ilimin addini dake magana. Hatta da shigar bayi hadimai da dogaran gidan yasha banbam dana masarautu da dama. Tsarin aurar da hadimai da bayi......gidajensu prison dinsu da makarantunsu.......komai nasu yasha banbam dana sarakunan qasar da dama. Omari bai samu damar cewa dashi komai ba.......babban saqon da yake qunshewa a cikinsa tun dazun ya fado masa "Shugaba yayi kira.........yace kuma lallai gobe mu sauka addis ababa". A nutse haisam ya waiwaya yana duban omari,saidai mamaki ya bayyana sosai saman fuskarsa. "Da gaggawa haka?". Kai omari ya gyada yana dubansa shima. " Yace bai sameka ta kowanne platform ba.....shi yasa ya ajemin saqon......ajemin saqon da ganin da nayi kuma dole ya sakani cikin operation din.......dama wannan shine burina,addu'ata ce ta karbu" Omari ya qarasa maganar murmushi yana subuce masa. Dauke dubansa haisam yayi daga kan omari fuskarsa na nuna alamun qaramin murmushi ta yankin rawanin da har yanzu bai saukeshi qasan fuskarsa ba. "Inaji a jikina kamar lokaci yayi......kamar wani abu ya bayyana game da abba *AJANI AHMED*" Yayi maganar da dukka yaqininsa. "Ka duba mana tickets da suke available daga jimma zuwa addis ababa......idan baka samu available ba ka sanarmin mu tafi a mota....." "Dama kafison hakan ai" Omari ya fada yana dan tsuke girarsa. Haisam bai waiwayo ya kalleshi ba......saboda yasan hade rai omari din yayi,sai wani lafiyayyan murmushi abinsa daya sake cikin rawaninsa. "Kuyi duba izuwa tasirin rahamar Allah yadda yake rayar da qasa bayan mutuwarta............haqiqa cikin halittar sama da qasa da sassabawar dare da rana akwai ayoyi ga ma'abota hankali......omari ka manta da wadannan ayoyin?". Kai ya jinjina omari din yana sakin murmushi alamun aah. "Akwai abubuwan lura da tunani da yawa akai kan ayoyin ubangiji......baka taba sanin hakan sai kayi yawo a duniya......ka keta dazuzzuga da tsaunuka......ka hadu da hadura masu yawa......abubuwan firgitarwa masu tsananin girma......ka tuna cewa duka mallakar madaukakin sarki ne......iya wannan kadai ya isheka ka qara imani da yarda da ubangiji" Kai sosai omari ya jinjina......shi kansa akwai surori cikin qur'ani da idan yana karantasu yakan tafi ne zuwa wata duniya ta daban ta zurafafa cikin lamarin ubangiji. 08187255862 A cikin jini da dabi'ar haisam suke........yana da bala'in son binciken boyayyun abubuwa irin wannan da suka shafi hikima da qudira ta ubangiji.......yana son nature sosai.......yana da son zuwa baqin gurabe muhalli da qasashen da baisan komai a kansu......qasashen da zai zama baqo da gasken gaske akan komai nasu.......baya da tsoro ko digo dis a ransa........baya tsoron shiga risk da hatsari kowanne iri ne......wannan shine ya zame masa sanadin shiga aikin masu bincike na farin kaya cikin sauqi wato Dss. Cikin qanqanin lokaci da fara aikinsa sai ya zamana kamar da experience dinsa ya shigo aikin gaba daya......wanda halitta ce a jininsa data zame masa dalilin samun qarin matsayi nan da nan......cikin shekaru kadan ya zama babba cikin NATIONAL INTELLIGENCE AND SECURITY SERVICE(NISS). Yakai matakin da zai zama shine na daya a wajen.......amma zuzzurfan tunani da kaifin hankali irin nasa ya sanya hangensa yakai kan abubuwa guda biyu. Na farko shi wanda yake akai a sannan ya fishi shekaru nasa ba kusa ba......sannan babban aboki ne ga mahaifinsa me martaba abba jifar.......ya riga ya sani,komai iliminka......komai wayewarka da saninka......akwai wasu dabaru da wasu hange hange da sai wanda ya baka shekaru zai iya hangensu........yana kunyar abba muhammad dawuud ya sauka a matsayi shi yahau kai.....duk da lokacin retired dinsa yayi.....amma ya nema alfarmar a barshi cikin office din yaci gaba da zama......shi zai zama a madadin mabiyinsa. Dalili na biyu......yakan ware wasu watanni a shekarar da qasar Ethiopia ke dashi da suka saba da namu watannin goma sha biyu......su din suna da watanni sha uku ne.....a ciki yana daukan wata daya yayi hutu,hutun da ba inda yake qarar dashi sai yin visa ya sayi ticket na wata qasar dake nesa da yankinsu da al'ummarsu.....masu babancin halaye dabi'u al'adu dama halitta irin tasu...... Wani lokacine da yake na musamman a rayuwarsa.......wani lokaci da yake jinsa na musamman shi kansa. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 17 Yana samun wani 'yanci......yana jinsa cikin tarin sukuni da sakewa.......babu wadannan hadiman a tare dashi........ba wadannan masu kula dashi din,hadiman da mooti ko sau daya baya yarda haisam ya motsa ba tare da ko mutum daya ba......illa idan zai shiga NISS,kasancewar wani sirrintaccen abune da ba kowa yasa ma'aikacin hukumar bane......daga shi sai karan kansa a irin wannan yanayin da yakeyin nesa da qasarsa da mutanensa. Yakan yi tilawar qur'ani sosai fiye da yadda ya saba saboda samun sakewa da sukunin zuciya. To muddin ya karbi wannan matsayin zai rasa wannan damar,dole ya zauna ya dinga bada umarni.......shi kuwa yana ganin kamar hakan koma bayansa ne kuma koma baya ga baiwar fikira da basirar da Allah ya bashi ce. Kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai idanunsu sun hange musu ita. Cikin hanyar data kadaita ga kowa. Sanye cikin wani wadataccen hijabi daya sauka ya lullube har saman qafafunta. Matashiya ce da shekarunta gaba daya ba zasu haura sha tara ba........lullube da wannan kebantacce kuma sirrintaccen kyan na 'yan asalin Ethiopia kuma 'yan qabilar Oromo.......wannan kyan da aka bar musu kayansu,hannunta dauke da wani madaidaicin kwali,idanunta kuma manne akan fuskar haisam din. "Saami" Omari ya fada qasa qasa,abinda ya sanya idanun haisam qiftawa yana saukesu daga kansa. Daga randa suka zauna sukayi sharhi da fashin baqi akan ayar da Allah yake magana akan LOWERING GAZE cikin qur'ani da suka yiwa take da yaren oromo da *Ilaalcha gadi buusuun* cikin qur'ani Allah yana cewa "Ka gayawa muminai su kame ganinsu kuma su kula da farjinansu......wannan shine yafi tsarkaka a garesu" Sai ya sake zama me tsantseni da kulawa sosai akan wannan din. Komai Allah yayi jan kunne gargadi umarni ko hani akai ba shakka akwai babban lamari da kuna batu akai......daga ranar da bincikensa yakai kai kuwa baya sake kusantar wannan abun. Ko kafin sannan mutum ne shi me tsantseni ta wannan bangaren......tun daha sanda ya mallaki hankalin kansa ya kuma fahimci irin halittarsa sai ya zamana ya dauki matakin kame ganinsa.......sake nesanta kansa daga dukkan wani jinsi da ba nasa jinsin ba......bai sha wahala ba,don dama dabi'arsa daban take.......tun asali kuma shi din mutum ne me kiyaye hakan,sai komai yazo masa da sauqi,har wani lokacin suna tsokanarsa da MR LOWERING GAZE. Wani lokaci su fada da turancin da dukkan su sun iyashi......wani lokaci kuma da yaren oromo din *Mr ilaalcha gadi buusuun* Qasa tayi da kanta,hakan kuma bai hanata takowa zuwa inda suke din ba,saidai ta rage saurinta sosai. Ta sanshi,sannan ta karanci abubuwa da yawa daga halayensa......wannan ya sanya dab da zasu isa ga junansu ta buda bakinta cikin nutsuwa. "Assalamu alaikum" Ta fada da cikakkiyar sallama. "Wa'alaikumussalam" Omari ya amsa yana niyyar wucewa,saidai tuni haisam ya riqe yatsunsa ya kuma dawo dashi baya. "Barka da warhaka" Saami din ta fada tana dan duban sashen da omari yake. Fuska yadan sake mata,a iya shigowarsa gidan yasan saami.......da fari bai dauki wani abu game da samee din ba da yadda take girmama haisam da damuwa da lamuransa ba.......sannu a hankali ya fahimci akwai wani babban al'amari a game da haisam din a zuciyar yarinyar. Tana da wata irin nutsuwa da kuma kamun kai..... Irin wadda ya jima bai ganta game da wata yarinya matashiyar budurwa me irin shekarunta ba.....wannan ya sanya shi kansa yake girmamata da kalar girmamawar da yaga haisam din yanayi mata. "Barka da dare" Ta fada tana dan rusunawa haisam din ba tare data iya kallon fuskarsa ba. "Barka.......ina zaki haka da daren nan a hanyar da ba jama'a?". Har tsakiyar zuciyarta taji tambayar da yayi matan.......yanayin yadda yayi tambayar da mamaki cikin muryarsa dake nuna da gaske baisan me ha fiddota zuwa ga hanyar ba a irin wannan lokacin.......bai fahimci ta fito bane kawai don ta samu ta ganshi ko yaya.......ta fito ne don ta kebanta dashi koda na daqiqa ashirinne. Bata iya ce masa komai ba,saita miqa masa kwalin hannunta,duk kuwa da yadda kunya ke dawainiya da ita. Kwalin yabi da kallo a nutse kafin ya maida dubanshi ga fuskarsa. Yanaso yayi tambaya ne game da kwalin amma sai omari yayi masa riga malam masallaci ta hanyar sanya hannu ya dauke kwalin daga tafukan hannayenta.......hakan ya bata damar juyawa ta basu baya sannan tace. "Saqo ne daga wata baiwar Allah" Daga haka ta soma takawa da hanzari tana bacewa ganinsu ta tsakanin wasu qananun bishiyoyi. "Wani lokacin sai naga kamar ta bangaren aikinka da karatunka kawai kanka yake kawo wuta..... Kamar ta fanninsu kawai kake gane komai". Fararen manyan idanunsa dake tsakiyar rawaninsa ya zubawa omari.........kamar zaice wani abu sai kuma ya fasa. "Tana buqatar ke kebe ne da ita fa.......kai kuma kayi kaman baka fahimta ba?......." "Na fahimta mana omari.....na fahimta" Ya amsa masa yana soma takawa yana yin gaba ba tare daya damu da sanin meye a kwalin ba. "Ba inda musulunci ya bamu daman kebewa nida ita irin hakan......ka manta ne omari?" Kai ya jinjina yana takowa don cin masa,duk da cewa hankalinsa yana kan kwalin daya dan budashi kadan yana leqa cikinsa. "Amma ya kamata ka fahimta.......ya kamata ka gane me yarinyar nan ke nufi......ko baka fahimta ba har yanzu sai anyi maka fashin baqi?". Kansa ya girgiza yana kafe hanya da ido kamar meson gano wani abu. " Na fahimta omari.......sameera sona takeyi.......so takemin irin na aure.....amma ni kuma........" "Karka soma cemin samee batayi ba......zanyi abinda ban taba yi maka ba wato qaryataka......kamar yadda nasan kaima kayi abinda baka taba yi ba wato qarya" Miskilin murmushin nan nasa ya saki,yana ci gaba da takawa ba tare daya dubi omari ba. Sai da yaja fasali sosai sannan ya maida masa amsa. "Tako ina samee tayi.......kamilar mace ma'abociyar addini.......mahaddaciya sittin da tafsir......wadda ta haddace litattafan addini masu tarin yawa,ba inda ta sani,daga gidansu sai makaranta.......sai nan gidan.......idanma akwai wani abu da samee bata cikashi ba......saidai cikar nan da ake cewa duk dan adam tara yake bai cika goma ba.......matsalar kawai ni dinne". Ya fada calmly har hakan na bayyana cikin maganarsa. Dakatawa omari yayi cikin mamakinsa. Ya dauka dukka daya jero wadannan maganganun zai gaya masa cewa ya jima shima da fara son samee ko accepting nata. "Kai din me?". " Ban shirya soyayya ba......ban kuma taba jin son samee a zuciyata ba so irin na soyayya......donme zan bata mata lokacinta?" Ya qarashe maganar da sigar tambaya yana kuma waiwayowa gaba dayansa hannayensa zube a aljihunsa yana zubewa omari su. Kallon kallo suka fara yi a tsakaninsu. Mamaki yana kashe omari.......yayin da haisam ke jiran ko zaiji wani qwaqwaran dalili da zai sanyashi bawa samee lokacinsa ko hankalinsa. Gaba daya ya gama gogewa omari hadda,sai yaja jikinsa kadan ya zauna saman kujerun concrete dake kusa dashi. "Sai yaushe kenan zaka shirya yin soyayyar......ka shirya kuma accepting wata?". Wannan boyayyen murmushin nasa dake cikin rawaninsa ya saki,ya kuma yi qas da kansa yana zubawa qananun fararen duwatsun da aka qawata wajen dasu idanu kamar yanason qididdige lokacin da zai jarrabawa wata macen ko ya bata dama a rayuwarsa. "Not now omari......ba yanzu ba,ina da sauren abubuwa masu muhimmanci daya kamata na gama dasu omari". "Haisam....." Omari ya kirashi a sanyaye yana aza dukka hannayensa saman kwalin.. "Ina jiye maka haqqin 'dubban 'yammatan da wannan shu'umin murmushin naka kadai ya jefa zuciyarsu kogin soyayya......ka kasa kuma taimaka musu da komai". Dole wannan karon murmushinsa ya fito da wani irin sauti. " Laifina ne omari?......" Kasa bashi amsa omari yayi......dondai da gaske kai tsaye bazaice laifin haisam bane.......hasalima dukka cikinsu yafi kowa takatsantsan da lamarin mata,banda jaruma kuma tsayayyar zuciyar da sukasan yana da ita tabbas ba abinda zai hanashi soma kiransa da ME TSORON MATA. Wani irin magnet ne cikin halittarsa dake fusgar hankalin 'yammata a kanshi........kusan dukkansu suna da irin wannan baiwar,amma nasa kaman yafi nasu zafi da yawa. "Karkayi kwantai ko kayi zaben tumun dare fa?......" Omari ya fada yana fidda idanunsa waje. Kai kawai haisam keta girgizawa kaman dariya nason qwace masa,fararen jerarrun haqoransa da haskensu ya fita harta qyallen bakinsa suka bayyana.......a wannan karon sai da yakai hannun nasa ya zame qyallen zuwa wuyansa don ya bawa dariyarsa damar fitowa sosai.......wannan ya sanya qarashen cikamakin kaykkyawar fuskarsa damar bayyana gaba dayanta. Wani lafiyayyen ajiyayyar baqa sidik din suma ce ta bayyana data gewaye habarsa da kumatunsa da wani iri qawataccen shape da zai gaya maka zallar qwarewa da sanin haqqin qasumba name askinsa. Kyawawan jajayen lips dinsa dake qyalli kamar an shafa musu man labba suka bayyana suna kuma sake zama ado ga jerarrun fararen haqoransa. "Ba damuwa.......sai na jira sanda d'iyarka ta farko zata isa aure saika bani ita". Wani harara omari ya watsa masa. "Ina ma ace akwai wani lafiyayyen abun bugu a nan?". "Kana da hannu fa omari?......abun bugun me kake nema?" Ya tambayeshi yana dage masa girarsa dukka biyun,amsar bayarwa omari ya rasa,daya tabbatar da haka sai ya zare hannayensa daga aljihunsa ya hardesu a qirjinsa yaci gaba da tafiya zuwa ciki hankali kwance. "Ko haka na zauna ba aure......Allah bazai tambayeni dalili ba.........muddin zan kare dokokinsa zan kuma tsare kaina......" "Ba zaka iya ba.......na rantse da girman Allah kana cikin sahun mutanen da aure ya zame musu wajibi" Omari daya miqe da sauri ya fada yana kuma bin sahunsa. Dariyar mamaki ta sake kama haisam,amma saidai bai juyo ba. "Zakayi kaffara omari......ka manta akwai manyan malaman da har suka rasu basuyi aure ba?......manya manyan malaman musulunci........ciki harda malamin mazhabar malikiyya imamu maalik?". "Na sani......inajin kusan lokaci guda muka karanta littafin daya kawo sunayensu gaba daya......malaman da suka fifita karatu akan aure........amma sam baka sahunsu fa" Dif haisam din yayi masa ganin suna dab da fara shiga gurin jama'a,kuma zuwa sannan haisam yana jin bazai iya ci gaba da musayar magana da omari din ba.......don yana cikin abinda ke burge omari dama can suyita musayar ra'ayi. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 18 ★★★Idan kaga yadda take shawagi cikin dokunan zaka rantse harda Allah ba diya mace bace,ba wasu alamu da zai nuna maka shakka ko d'ari d'ari game dasu...... Daya bayan daya take zagayawa tana duba lafiyar dawakan nata guda uku cikin dokunan hawa shida da take dasu. Uku a agadez tare da raqumma uku da takan hau lokaci bayan lokaci,sai wadannan guda ukun da take dasu a nan Niamey. Wasu irin qosassun fararen dawakai da take matuqar sonsu........ba ita kadai ba......duk wanda yasan sirrin kyan doki bazai kallesu sau daya tak yaji basu burgeshi ba. Sanye take da yalwataccen wandon palazzo data dora masa wata blouse a sama long sleeve,sai ta kawo top data sauka har saman cinyoyinta me gajeran hannu ta dora a sama. Lallausan scarf ne a kanta data nannadeshi kamar tufkar igiya tayi wani irin dauri dashi daya bawa doguwar sumarta dake kwance a bayanta daman fitowa sosai,saidai ba zaka samu daman ganin tsahon sumar daya bazu a gadon bayanta ba sosai saboda wannan top din data dora a saman gashin nata. Wani takalmi ne a qafarta,samansa kaman socks yake,qasansa ne takalmi. Jikinta a kowanne motsi idan tayi lallausan qamshinta ne yake kadawa. Miqewa tayi daga tsugunnon da tayi tana duba qafar daya daga cikin dawakan nata,ta juya a nutse tana duban gabjejen mutumin dake tsaye a bayanta cikin son cika umarninta. "Thunder zan hau(sunan daya daga cikin dawakan nata)" "An gama ranki ya dade" Ya furta cikin rusunawa yana sakin murmushi. Da ita za'ayi wasan tseren dawakan.......amma ya fita qaguwa ranar tazo. Karon farko kenan data taba yin register kuma zata shiga wasan,duk da irin qwarewarta a sarrafa doki da kuma raqumi. Akwai kyakkyawar alaqa tsakaninta da dabbobin nan guda biyu,ta taso a cikinsu sosai,ta kuma koyi hawansu da sarrafasu. Tana da tarin raquma da ake kiwata mata,amma a ciki guda uku kacal take hawa da aka waresu musamman suka kuma saba da juna. Hakanan dawakanta guda shidan nan na Niamey da wadanda suke a agadez tana bala'in ji dasu. Sam sam yadda ta damu dasu bata damu da motocinta ba.....bata muhimmanci ba kamar nasu. Wayarta ce dake cikin aljihun wandonta tayi qara,ta zura hannunta ta dauko tana duba me kiran,abinda ya saka murmushi subucewa daga fuskarta kenan,ta fara takawa tana fita a wajen hadi da sanya wayar a kunnenta. Daga yadda take amsa wayar kawai zai shaida maka da wani me muhimmanci take magana.......hankalinta kwance take barin sashen dawakan zuwa parlor din gidan da wayar a kunnenta. A nutse ta murza handle din parlor din ta wuce ciki,daga baki bakin qofa ta zare takalmin qafarta ta sauyashi da wani,sannan taci gaba da shigewa zuwa main parlor na farko. Shehnaz kadai ta gani saman dining da alama lunch take. Don yau tun safe bataga gilmawarta ba,duk da kwana biyun nan ma ba wani magana sukeyi sosai ba. Haushinta takeji akan Jamaal shi yasa take shareta......tana ganin sam bai dace shehnaz ta ragi rayuwarta damarta kimarta da martabarta ba wajen auren jamaal din ba.....wayayyen namiji tafi dacewa dashi......wayayyen namiji take da buqata ba jamaal ba. Sai ita kuma shehnaz din tayi kamar bata gane abinda yake faruwa ba......sam taqi ta nuna wata alama na ta fahimci akwai wani abu. "Munyi magana da mommonki morsa safiyya......." Daga daya bangaren wayar mata da suke kira da Nannie ta furta da muryarta me cike da nutsuwa. Lumshe idanunta akhnan tayi tana dawo da tunaninta kan wayar da sukeyi da Nannie din. Kiran sunan morsa safiyya kadai kuma ya dawo da nutsuwarta jikinta. "Me matar nan taje ta fadawa Nannie a kaina ne?" Akhnan ta raya a ranta kafin ta sake jin maganar Nannie din. "Na bawa shehnaz saqo......ina fatan ta gaya miki ko?". Sai data aza idanunta akan shehnaz dake kai abinci bakinta tana kuma danna waya da daya hannun kafin ta dauke idanun tana ansawa Nannie " Aah Nannie.......batace komai dani ba". "Don qaniyarta ban gaya mata ta gaya miki ba?" Nannie ta fada da alamun daukan zafi kadan a muryarta. Kai akhnan ta karyar gefe jin Nannie din zata dauki zafi da shehnaz,duk yadda sukakai ga fada da junansu basason wani yaga laifin dan uwansa,don haka a shagwabe tace. "Fada mukayi Nannie.......batason kulani shi yasa bata gayamin ba......" "Yoni ina ruwana da wannan shashancin naku da zata saka maganata a ciki?....." "Nannieeeeee.....bada gangan bane ba" Akhnan ta sake fada a narke kaman zata sakewa Nannie din kuka. "Sannu me 'yar uwa........ni naga gyada ma sarkin goyo" Nannie ta fadi tana jin haushin yadda ko laifi akayi tsakanin su ukun ake rasa gane waye me laifin waye me gaskiya. "To abinda na gaya mata ta gaya muku......naji fes abinda ya faru zuwan yaroncan na garin tahoua........wannan shashancin ya ishemu hakanan......kuma tabbas don bana agadez wasu abubuwan ke faruwa,nace ta gaya miki keda aisa din gaba daya......Ku maida hankulanku jikinku......lokaci yayi da zamu miqaku dakunan aure.....don ba zamu zuba idanu ku dinga rayuwarku yadda duk kukaso ba". Duk wani walwala da nishadi da ta tashi dashi a yau Nannie ta warware mata shi tas,sai kawai tayi shuru tana sauraren sababin da Nannie din takeyi harta gama. "Sai anjima" Nannie ta rufe da fada tana katse kiran. Ba yau ko jiya ki shekaran jiya tasan Nannie ba.......tsayayyar mutum ce me wani irin kafaffen ra'ayi.......tana tsananin sonsu da qaunarsu.......to amma a hakan fa idan abunta ya motsa kowa ma bi take ta kanshi. Qanwa ce guda daya tal data ragewa sultane muhamma hamud a duniya,kuma itace mahaifiyar aisa.......mahaifiyar shehnaz ke bin Nannie,kuma shehnaz kawai ta Haifa ta rasu,don haka shehnaz Nannie kawai ta sani a mazaunin mahaifiya. Sunan Nannie na asali bilkissou......Nannie ya samo asali ne daga bakunan shehnaz da aisa. "Soni masoyi......soni ka sani ranka.....domin so da yardaaaaaa" Muryar aisa da akhnan batasan da zamanta a gefe ba ta soma motsawa cikin baitocin waqoqin fitacciyar mawaqiyar qasarsu. A nutse ta juya tana duban aisa din,ta tabbatar da ita take......kuma da biyu tasan takeyi. Rasa me zatayi mata tayi,kawai saita jefeta da wayar hannunta. Dukka idanunta aisa ta fidda bayan wayar tadan sameta a qafa kadan tana bin wayar da kallo kafin ta kalli akhnan. "Vous ne savez pas à quel point elle est coûteuse(bana tunanin kinsan tsadarta),kike jifa da ita haka?". Manyan almond shape eyes dinta ta ware ta watsawa aisa din,saidai kafin suce komai shehnaz dake can a zaune ta fara magana a nutse "Vous êtes tous invités aux courses de chevaux spéciales, présentation du nouveau cavalier de la famille royale, Akhnan Muhammad Hammud". Yadda tayi shuru bayan ta kammala karantawa haka falon ya dauki shuru,kowa a cikinsu ya rasa me zai fada. Tsam akhnan din ta miqe,don batason kowa a cikinsu ya maido mata tunaninta baya,da nutsatsiyar muryar nan tana da ta dace da innocent fuskarta da sam bata dace da attitude nata ba taurin kanta da kuma kafiyarta ba tace. "Tous sont invités(eh.....dukkaninku ana gayyatarku" Sai ta fara wucewa hankali kwance. "Biftu.......sanarwa ne fa na gasar tseren doki fa aka karanta miki.....da sunanki da na sultane a mazaunin babbar baquwa 'yar tsere......what if me martaba yaji?". Zagayayyun idanunta ta juyo ta zube musu. "Idan ke kika gaya masa ba......ba wani gurin bane.....cikin Niamey ne......cikin Niamey din ma cikin hippodrome.....ba wani bangon duniya ba". "Tare da maza ne fa biftu" Aisa ta sake fada fargaba na bayyana saman fuskarta. "Et puis?(sai me?).....C'est mon rêve(mafarkina ne),zan kuma cikashi ko sau daya ne". Ta fadi hankalinta kwance,bata kuma qara ba taci gaba da takawa tana tafiya abinta. "Laissez-la(ki qyaleta).....ki barmu muga wasannan s'ilvous plaît(please)" Shehnaz ta fada tana murmushi,don har ga Allah ita abun ya mata dadi. Tana ganin ba wani abu bane me muni tunda na dan lokaci ne,kuma tafi kowa sanin yadda akhnan ke mugun son tseren doki da yadda ta qware akai. "Na qyaleku" Abinda aisa kawai ta fada kenan ta koma tana zama ba tare data sake cewa komai ba. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 19 Sanye yake da Moroccon jallabiyya ta maza,wadda ta sa haskashi sosai tayi masa wani irin kyau tana kuma sake haska fatarshi dake da wani irin launi,shi baiyi haske me yawan da zai kashe maka idanu ba,hakanan baiyi duhun fata ba,don kusan launin fatarsa yadan saba kadan data ainihin 'yan qabilae oromo. Lallausar baqar sumarsa me santsi irin ta 'yan qabilar oromo din sai wani sheqi takeyi da walainiya,sumar da ta take kwance saman kansa zuwa gefe da gefen fuskarsa da kuma habarsa. Kansa wata qaramar hula ce irin ta larabawan morocco,wanda hakan bai hana bayyanuwar baqar sumar tasa ba data yiwa fuskarsa wani irin ado. Shi daya ne cikin dakin,wanda kai tsaye ya amsa sunan library me wani irin tsari me daukan hankali da gasken gaske. Wani irin ma'ajiyar litattafai ne kewaye da ita,dauke da tarin litattafan da suka wuce ka iya qididdige yawansu,domin kuwa kowanne bango sune......bangon kuma tun daga samanshi har qasanshi. Akwai litattafan dake rubuce da yare kala kala......tun daga kan English......french.....oromo.......yayin da litattafan addini na larabci suka mamaye kaso mafi girma na library din. Komai na library din ya bada wani irin yanayi da nature me kwantar da hankali da daukan hankali,gurine da yafi kowanne guri sama masa nutsuwa a duniya.........baya ji a jikinsa akwai wani abu daya mallaka da yakai wannan library din muhimmanci a wajensa. Yana iya rayuwarsa shi kadai a wajen.......zai iya qarar maka da awanninsa na rana duka a wajen ya kebance kansa. Karatun addini ruhinsa ne......fatarsa ne.....kuma rayuwarsa ne,ya kuma sameshi,don babu wani abu da yake sanyashi nishadi kamar lokaci irin wannan. Lokacin da zai kebanta cikin yanayi na shuru da wata irin kyakkyawar nutsuwa cikin dakin karatun,yana yin bincike da zaqulo mas'aloli masu yawa daga mazhabobi da malamai iri daban daban. Ya tsara wajen daidai da yadda zai dace da tsarinsa da kuma yanayinsa da abinda yafiso. Wasu irin kujeru da lausasan carpet aka yiwa gurin ado dasu,sai wani sashe na daban na library din da aka sake zuba wasu rukunin kujerun da kuma teburansa,yadda zai dace da zaman me bincike. Daga gaban kadan dan qwarya qwaryan table ne me dauke da wasu qananun cabinet,wanda ba komai a ciki sai nau'in coffee kala kala.....coffee makers har biyu da wasu irin mugs da trays masu daukan hankali. Yankin jimma dama qabilar oromo gaba daya coffee yana daya daga cikin manyan al'adunsu.......sukan ware babban fili me girman Hector me yawa suyi noman coffee zallah. Su kullum ranar shan coffee ce a wajensu bayan rana ta musamman da suka ware mata,ba abinda yake da muhimmanci a gurinsu irin coffee. Wannan jinin da wannan al'adar ta gudana a jikinsa sosai,don ko cikin masu son shan coffee din shi na daban ne. Sake miqe dogayen qafafunsa yayi saman ottoman sofa dake gabansa yana fidda wani sassanyan numfashi. Sosai yake jin dadin zaman nasa a nan safiyar lahadin,duk da rabin hankalinsa yana kan wata 'yar qaramar danja dake gefansa. Green light da yayi blinking shi ya sakashi daga kansa a hankali,lumsassun idanun nan nasa suna sake rusunawa da wata irin nutsuwa yana duban light din don tabbatar da motsawar da yayi. Ya sake bada green color kuwa......don haka ya sauke qafafunsa a hankali yana rufe littafin bayan ya sanya alama,ya miqe da cikakkiyar nutsuwarsa yana zare hular kansa ya ajiyeta saman ottoman din,sannan ya dauki wani irin nau'in Bluetooth ya latsashi ya sakashi a kunnensa yana nufar wata bookshelf data banbamta da nau'in da yanayin kowacce daya dake wajen,labbansa masu sulbi dake da wani irin color suka motsa a hankali suna bada sautin husky voice dinsa da ta rage boldness yana fadin. "Assalamu alaikum warahmatullah" Daidai sanda ya latsa wani abu jikin bookshelf din take ya juya kansa ya canza siffa daga bookshelf zuwa qofa,sai ya murza handle din ya shiga sannan ya maidata yadda take bookshelf a dazu. "Wa'alaikumussalam.........mun tashi lafiya haisam?". Babban mutumin da muryarsa kadai ta bayyana nutsuwarsa da dattijankarsa ta bayyana sosai ya fada. "Alhamdulillah babbo". Ya amsa yana kunna switch na dakin,take haske ya mamaye ko ina. Wani lafiyayyen daki ne da tun daga gininsa zaka tabbatar ya samu ingantaccen tsari da wannan irin sirri na musamman,don hatta da windows din dakin suna da wani irin yanayi ne,ba normal winduna na yau da kullum bane. Cike yake da tarkacen kayan wuta iri daban daban......wayoyi tsayayyu alluna na zane.......da sauran wasu abubuwan da ko sunansu ba lallai ka sani ba. Saidai duk da wannan kayan komai yana ajjiye a muhallinsa a kuma tsare,don a kallon farko ma abinda zai fara zuwa kanka shine wani office ne na musamman dake koyar da harkar na'ura me qwaqwalwa. "Nayita qoqarin samunka a jiya......sai omari na barwa saqo.......ka duba email naka yanzu yanzu". "Okay bobbo". Ya amsa masa a girmame yana danne makunnin Bluetooth din nasa sannan ya isa a hankali gaban wata qaramar system yaja kujerar dake gabanta ya zauna. Waving hannunsa kawai yayi a fuskarta ta kunna kanta da kanta,ya matsa gaba sosai ya fara sarrafata. Wasu irin tarin password ya saka mata kafin ya budeta,password din da zakayi mamakin yadda akayi suka zauna daram cikin kwanyarsa. Wata irin nutsuwa ya bawa na'urar yana bin kowanne saqo daya bayan daya da idanu da kuma hankalinsa,nutsuwar da zata gaya maka muhimmancin aikinsa a wajensa da yadda komai na aikinsa yayi masa ya dace da tsarinsa da muradinsa. Hasken screen din ya sake haska fararen idanunsa da suke juyawa a hankali cikin screen din,har zuwa sanda ya kammala duba saqon. Bayansa ya jinginar jikin kujerar yana yin relaxing sosai,still bai dauke fararen idanunsa daha kan allon computer din ba. Yatuntsa guda uku cikin sumar dake kwance saman habarsa yana dan yamutsasu a hankali. Paragraph din qarshe na saqon da bobbo ya rubauta masa da kalmar turanci ya motsa labbansa a hankali ya karanta *_operation into AGADEZ_* Ya kafe kalmomin da idanu yana maido tunaninsa baya. Duk tsahon wadannan lokutan?,duka tsahon shekarun?,me yasa tunaninsu da bincikensu baikai can ba sai yanzu?. Idan zai iya tunawa shine ya fara kawo wannan idea na baza komarsu zuwa ga qasashen dake cikin fadin africa gaba daya. Bai manta osama yana daya daga cikin mutanen da sukayi Challenging nasa a lokacin......saboda dalilai na ganin cewa duka duka yaushe ya shigo hukumar tsaro ta sirri?......bai wuce watanni da fara aiki dasu ba amma ya samu nasarar shigowa babban team irin nasu na goggaggun ma'aikatan sirri.......ya tsinci kuma case din kisan gillar Abban ajani Ahmed......duk da akwai abota me qarfi da girma tsakaninsa da mahaifinsa me martaba abba jifar,amma osama yana ganin wannan daban da wannan. Ya raina tunaninsa a wancan lokacin,yana kallonsa a wanda baisan komai ba akan aikin........taka haye ne shi. Ran osama yayi fari qal a sanda aka soma fadada binciken zuwa wasu qasashen Africa din.......kuma basu samo komai a kai ba.......sai matsala ma da yaso jawowa ta alaqar diplomacy tsakanin Ethiopia din da maqwabtanta. Daga qarshe bobbo yace a haqura a ajjiye binciken......aci gaba da taba case din lokaci bayan lokaci. Yana da wani abu guda daya a rayuwarsa daya zame masa silar nasararsa.........JAJIRCEWA DA TSAIWA akan dukkan abinda yasa a gaba,ya kuma samu gamsuwa cewa eh zaiyi. Baya tunkarar komai da ka,sai ya gabatar da ISTIKHARA irin wadda ma'aiki ya koyar da sahabbansa......sannan ya dora da addu'o'i. Wasu lokutan harda azumi,muddin ya gama wadannan ya samu nutsuwa da gamsuwa akan komai.....to ko meye wannan abun,komai girman hatsarinsa baya jin fargaba ko digo akai,domin yasan Allah ya bawa zabi......kuma ya gama zabar masa koma meye..........so bashi da wani sauran haufi tsoro shayi ko shakka. Tun daga wancan shekarun bai qara bari zuciyarsa da jikinsa sun huta ba akan case din ajani Ahmed.......musamman daya zama aboki sosai ga mooti abba jifar........wannan sai yake sake motsa zuciyarsa a duk sanda hira ta hadashi da me martaba zancan ajani Ahmed ya fado ciki. Komai yayi farko yana da qarshe.......kamar yadda akace komai nisan jifa qasa zai fado......komai girman gona kuma akwai kunyar qarshe.........cikin watan daya wuce yana tsaka da bincikensa game da wanda dukkan hukumarsu ke qarfafa zato a kansa. Ya samu wani irin haske daya sanyashi jimawa yana duba bayanan gami da hadesu da wasu bayanai dake ajiye a kwanyarsa. Ya ajiye bayanan yana musu kyakkyawar ajiya......sannan ya miqe ya daura alwala yayi sallah,a sujjadar qarshe kuma ya jima yana ganawa da ubangijinsa ta hanyar karanta la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin. A wunin ranar duka ya lazumci istigfari da ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagis. Aiki ne me hadarin gaske daya tabbatar samuwar nasararsa wata samuwar nasara ce me zaman kanta ga gwamnatin Ethiopia. Mutuwar abba ajani Ahmed ta kusan zamewa gwamnatin Ethiopia gaba daya barazana......kasancewar abba ajani Ahmed mahaifinsa dan asalin qasar America ne......kuma shi kansa acan aka haifeshi,don haka halalin qasar ne.......kasuwanci ya dawo da mahaifansa qasar Ethiopia shekaru masu yawan gaske a baya,har suka rasu suka barshi da tarin nashi iyalin har zuwa sanda ajalinsa ya riskeshi shima. Bashi da kokwanto akan bobbo game da case din......amma addu'ar da yayin ta sake saka masa nutsuwar bobbo ya sani. Ya jima shuru yana duban haisam bayan gabatar masa da dukkan bayanan. Ya rasa me zaya fada a kanshi?. Tabbas yana ji a ransa irin haisam din duk bayan qarni guda ake haifar mutum daya irinsa. Jajirtacce dan kishin qasarsa al'ummarsa dama iyayensa. Kafadarsa ya dafa yana jin zuciyarsa tana narkewa. "Ina sake taya mooti murnar samun d'a kamarka haisam.......kaidin wata kadara ce me tsadar gaske.......ko yau ko kuma a iya nan ka ajjiye aikinka tabbas qasarmu zatayi alfahari dakai". zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 20 https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX "Ya rahman......ka sanyi na kasance mafi alkhairin abinda suke zato(wannan din addu'a ce me kyau daya kamata ka dinga yi a duk sanda aka yabeka game da wani abu,ita annabi ya koyar)" "Zanso na aiwatar da aikin nan qwarai bobbo" Haisam ya furta a sanda muhammad dawud(bobbo) ya bashi tabbacin sahalewa aiwatar da aikin. Idanu muhammad dawud ya zuba masa,yana yawaita mamaki sosai akan yadda haisam keson aikinsa da yawa. Tabbas ba shakka national intelligence and security service sun bashi wani girman matsayi......sun bashi albashi me kyau da yawan daya kusa daidai dana shugana qasarsu.......yana da masu tsaron lafiyarsa.......to amma dukka wadannan ya samesu dama tun daga gidansu,ya samesu tun kafin ya shigo NISS......gata da soyayyar daya samu daga gida ta ninka wannan. YARIMA ne da kowanne lokaci zai iya zama sarkin jimma.......mallakin hamshaqiyar fadar ABBA JIFAR amma duka ya watsar da wannan ya rungumi aikin da matsayinsa ya haura wannan inda yazo cikin masu wannan dabi'ar. Eh......tabbas,duk wanda ya kalli haisam a ganin farko zaisan cewa wannan jinin na SARAUTA yana harbawa a kowanne sassa na jikinsa.......akwai wannan QASAITAR da IZZAR a tare dashi,don sarauta ba qarya bace......duk qanqantarta saika samu tasirinta cikin jinin ahalinta.....ballantana babbbar masarauta me dimbin dukiya da arziqi irin ta JIMMA. Yana da wani irin kwarjini da akan samu akasarin ahalin sarauta dashi.......yana da irin nasa jin kan wanda nature dinsa ne bawai yana yi bane don gwada shi wani bane.....don ya karanta yasan kuma illar hakan.......amma kuma kyakkyawar mu'amalarsa da dukka wanda yake sama dashi.......tausayinsa da jin qansa ga masu rauni ko wanda yake qasa dashi na dabanne. "An baka dama haisam.......amma wannan tafiyar tafiya ce me hatsari.......don hatta da gwamnatin qasar NIJER da hukumominsu bamu yarda susan da shigowarka qasar ba......zamu dan take wasu dokoki na qasa da qasa saboda mu samu cikakken sirri......don haka yana da kyau ka shaidawa mooti........har nanay itama". Ya gamsu da batun gayawa me martaba.......amma nanay fa?,baisan ta ina zai fara fahimtar da ita ba. Zuqe numfashinsa yayi ya fesar yana maimaita sunan garin......bazaice bai taba jinsa ko jin sunansa ba.......amma basa cikin garuruwan daya dauka suna existing suna kuma da wani manyan abubuwa da bincike ko wani aikinsu zai iya rabawa ta wajen. Shi duka bincikensa NIJER ya gani.......baisan ya akayi cikin NIJER din ba kuma ya fada wani gari wai agadez ba. Cikin qwarewa da iya sarrafa na'ura ya koma kan system din,ya tura bobbo komai yana shaida masa yau din zuwa azahar zasu sauka a addis ababa in sha Allah shida omari,ya qarasa tura masa komai,sannan ya fita daga system din ya kasheta gaba daya. Kowanne qwan lantarki sai daya kasheshi,ya maida dakin yadda yake sannan ya dawo bakin wannan qofar me siddabaru ya fito ya dawo ainihin parlor din da ya fita cikinsa a dazu. Kusa da littafinsa ya koma ya daukeshi hade da wayarsa,ya taka zuwa wata ma'ajiyar litattafai dake parlor din wadda yakan dubasu a iya parlor din ya sakasu a ciki yana duba fuskar wayarsa. Fararen idanunshi ya zaro waje.......kiran da bai samu daman dagawa ba na nanay ya gani har uku,sai ya kalli lokaci sannan ya juya ya dauki wayarsa ya maida saman kansa yana dosar qofar fita daga parlor din. Wani courtyard ya bulla me ban shaawa da aka cikashi da tsirrai bisa tsari me burgewa,sannu a hankali ya sake fadawa wani balcony sannan ya bulla wani setting room din kafin ya tadda doguwar veranda da zata sadashi da ainihin sassan nanay. Wani irin gini ne musamman da yafi kama da gine ginen mutanen sin wato CHINA fadar abba jifar ke dashi......shigen gine ginensu sak da sak da sai kayi tunanin a qasar sin din kake. Yana takawa da cikakkiyar nutsuwa da dadin da iskar safiyar tayi masa......zuciyarsa na shirya masa yadda zai fahimtar da nanay tafiyar ba tare data daga hankalinta ba. Tun a jiya suka raba dare suna magana da me martaba.......ya gama fahimtarsa,ya bashi goyon baya kuma d'ari bisa d'ari,saidai ya jadda masa yaci gaba da riqe addu'a.......ya kula sosai.......ya kuma rage jefa kansa cikin abubuwa masu hadari har haka. Cikin girmamawa dukkan wani hadimi da suka hadu saman hanyar yake gaidashi da wani matsanancin martabawa. Baya gajiya haka yake amsa musu cikin kulawa shima,mata a cikinsu ne kadai yake dagawa hannu ya wuce. Sannu a hankali ya cimma farfajiyar sassan farko na nanay........,tun bai kai ga qarasawa ciki ba daddadan sautinta ya soma sauka a kunnensa da irin qir'arsa sak. Idanunsa ya lumshe ya kuma budesu yana jin wani yanayi yana ratsashi. A duniya babu wani sauti mafi girma.......sauti mafi saukar masa da dukkan nutsuwa irin sautin karatun qur'ani. Ba wani abu dake sauke fushinsa.......yake dawo da nutsuwarsa gangar jikinsa irin sautin qur'ani. Ba wani labari dake masa dadi a kunnuwa idanuwa da zuciya irin ya bude qur'ani......surorin da Allah madaukakin sarki ya saukar dake bada labarai na al'ummar da suka wuce.....labarai na annabawa da sauran abubuwa na rayuwa. Cikin tsari daliban nata da suka kasance hadimai ne na sassan nanay suke zaune a gabanta. Kowaccensu sanye da yalwataccen hijabin daya sauka har qasa,wanda da kudinsa ya bada kwangilari dinkin kyawawan hijaban har guda dari da suka kasance launin Sacramento green me kyau. Samee din data kasance malamarsu a kowanne ranakun mako irin wadannan guda biyu tana zaune saman wata gajerar cushion chair maras tudu,tana sanye da farin hijabi qal kamar hannu bai taba sauka a kansa ba. Baka ganin komai nata sai kewayayyar fuskarta da manyan idanunta dake yawo tsakanin ayoyin qur'ani. Wannan din wani ginannen burinsa ne daya taba furtawa nanay......burin ilimantar da duk wasu hadimai da bayi dake sassanta dama gidan gaba daya da ingantaccen ilimi daga qur'ani cikin sanin fassararsa da kuma tarin ma'anonin da yake dauke dashi. Yayi maganar ne a sanda samee ke shigo cikin parlor din wajen nanay.......ashe kuma taji,kafin yakai ga zabar malamar da zata kasance malamarsu sai zuwa yayi wani hutun qarshen mako ya samu samee din ta fara gabatar da karatun. Idan yace baiji dadi ba yayi qarya......idan yace girmanta da kimarta basu dadu a idanunsa ba yayi qarya,don haka sai ya bada kwangilar dukka hijaban da zasu sanya harda malamar tasu. Yaransu yasa an tashi makarantar islamiyya gagaruma cikin gidan,wadda ta zama kyauta kuma sadaqatul jariya ga kowa,har yaran dake wajen masarautar. Mazajen gidan kuma ya kawo malami namiji da zasu dinga nasu karatun juma'a da asabar........yawanci asabar din shi yake zama yake musu litattafai guda biyu na fiqhu da hadith saboda inganta ibadarsu bayan qur'anin,wannan ya sanya itama samee ta saka ma matan littafin qwaya daya na fiqhu.....bayan sun saukeshi kuma take sanya ran saka musu hadith koda me hadisai darinnan ne. A cikin jikinta taji akwai wai baqon abu me kaifi a wajen........a cikin jikinta taji wata baquwar halitta ta wanzu a wajen,don haka tana kaiwa qarshen ayar suka kama suna maimaitawa,saita daga idonta a hankali take suka fada cikin nasa. Wannan qaqqarfan maganadisun ne taji ya fusgeta da wani irin qarfi,wannan kwarjinin nasa daya sanya gumi tsatsatsafo mata ta cikin hijabinta......wannan kyan nasa daya zame mata tamkar wata jarrabawa ya ratsa idanunta,duk sai taji wani abu yana tsumata,musamman a yau data samu damar ganin Fuakarsa gaba dayanta ba tare da suturtaccen mayanin nan nasa ba.......a kuma safiyar da dakusashen hasken rana ya bayyana fuskarsa tarwai. "Subhanallah" Ta furta qasan ranta sanda ya sake mata dan siririn murmushin da iya labbansa ne kawai suka motsa,yana alamta mata jinjinawarsa,sannan ya juya a nutse yana bin qofar da zata sadashi da nanay din. Sai data rasa numfashinta na wasu daqiqu kafin ta samu kamoshi,inda ta godewa Allah ta gaya biya musu suna maimaitawa ne tana musu gyaran inda suke da kuskure. Can qasan ranta tana tuhumar kanta da kalar tuhumar da har yau bata daina yiwa kanta ita ba. Me yasa ta jarabtu da kyansa?,me yasa ta jarabtu dashi?,daidai ne ta sakarwa zuciyarta linzamin kyau ado da qawa kuwa?. Ta sani yana da wasu qualities da ba ita kadai ba.......mata da yawa dake kewaye dashi sunsan yana dasu.......ya mallakesu ya kuma samu baiwa dasu......to amma a karan kanta me yasa kyansa yake zama barazana a gareta?. Akwai wani ra'ayinta guda daya da take dashi,bataso ta cusawa haisam kanta.......bataso a mishi tayinta......bataso kuma ya sota saboda wani abu na daban,tanaso ya sota da kansa......tanaso ya sota don ta cancanci ya sota din. Tana karantarsa sosai,duk da cewa yawa yawan zamansa ba a jimma bane.....a addis ababa ne,zuwansa sai weekend,amma duk da haka ta karanci abubuwa da yawa a kansa. Har yanzu bataga alamun da takeso take kuma sanya ran ganinsu a tare dashi a kanta ba,saidai ta sanya a ranta zataci gaba ta dukka hanyar data dace. A nutse ya sake jaddada sallamarsa a parlor din kaman yadda ya saba a duk wani guri da zai shiga. "Wa'alaikumussalam" Matashiyar budurwar dake zaune saman doguwar sofa ta amsa tana daga kanta. Qaramin murmushi ya subuce mata,ta miqe daga zaunen da take tana duban haisam da yake shigowa da kyawawan idanuwanta da suke kama dana haisam din. Wanda banda su ba abinda ta dauko na kammaninsa,saidai ko tsaho da nata yafi bayyana saboda jikinta baikai nashi murjewa ba. "Akkam bulte(barka da safiya)" Ta fada murmushin nan yaqi barin fuskarta "Akkam jirta rumaisa(kina lafiya rumaisa?" "Alhamdulillah captain sheik" Rumaisa ta fadi tana murmushin daya sanya haisam yasan lallai akwai wani abu a qasa,musamman data kirashi da wadannan sunayen a jere haka guda biyu. "Ehheeenn" Ya fada yana dage dukka girarsa biyun sama,abinda ya qara masa kwarjini kenan har a idanun rumaisa. Kai ta girgiza tana rage kaifin murmushin ta. Ganin data sama a ya zun da yadda Moroccan abayar jikinsa ta dace da zubi da tsarinsa,sai maganar daya daga cikin qawayenta me suna anniisa ya fado mata. Kusan sallar isha'i ta daren ranar da akayi irreecha festival yabar baya da qura......don qira'arsa ta tayar da sirrin boyayyun zukatan dake cike da boyayyar soyayyarsa cikin qawayenta. Ganin kamar bata shirya gaya masa ba sai ya kauda zancen yana tambayarta "Nanay eessa jira?(ina nanay?)" Da hannu ta nuna masa bangaren dakunanta na musamman da banda iyalinta ba wanda yake da hurumin tsallakewa har nan. "Tana ciki bata jima da shiga ba" Baice komai ba ya fara takawa,sai muryar rumaisa ta dakatar dashi. "Obbo captain(sir captain)". Sunan da sukafi kiransa dashi. Dakatawa yayi daga tafiyar da yakeyi wadda rumaisa ka qarewa kallo tana kuma sake gasgata zancan anniisa "Yana da wani irin taku na daban.......qasaitarsa tafi taku.....kuda kuke mata amma shine yake da jan ajin da izzar". Hararta kawai tayi a sannan,don itakam obbo haisam ba zata iya cewa ga wani sanda ta tsaya qarewa takunsa kallo ba. Eh har gwara maganansa,ita kanta wasu lokutan idan yana magana burgeta yanayin tsarin maganarsa takeyi cike da ginshira......amma tafiya kam a yau itama ta shaida hakan. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 23 ____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki _____________________________ *_Addis ababa bole international airport(ADD)_* Tafiyar awa daya da mintina biyar ta kaisu babban birnin na Ethiopia wato addis ababa,wanda cikin qasa da minti talatin ya kammala komai suka baro airport din qarqashin kulawar security din dake bashi tsaro cikin addis ababa din. Kazanchis layout suka nufa......unguwar da ya mallakin gidan zama na kasan kenan bayan gidan da hukumar binciken sirri suka bashi. Unguwa ce data hada manyan mutane da qusoshin gwamnati. Baqi 'yan qasashen waje da kuma manyan ma'aikatu na alaqa tsakanin qasashe da kuma hukomomi manya na tsaro. Gida ne dake da wani irin tsari da zai baka sha'awa qwarai,qaramar villa ce da batayi wani girma na azo a gani ba......amma tana da girman da za'a iya sanya matan aure hudu a ciki suyi rayuwa cikin walwala da sakewa. Ganawa da ma'aikatan gidan shine abu na farko da yakanyi a duk sanda ya dawo.......yau dinma hakan yayi,saidai batayi tsaho ba,kasancewar yana sanya ran daga yanzu zuwa kowanne lokaci zai iya fita zuwa headquarter dinsu dake cikin kazanchis din. *_AGADEZ_* *NIAMY* Tsaf ta kammala shirinta cikin wani kebantaccen guri na nusamman da aka bawa 'yan wasan dake filin gudanar da wasan don shiryawa gabanin fitowarsu. Wata irin shiga data sake fidda ainihin kyanta,wanda hatta da aisa da Shehnaz zama sukayi suna kallonta. Farin skinny trouser daya fidda shape na qugunta da sosai......wata irin jacket data dora samansa me dogon hannu bayan riga 'yar ciki data saka. Ta daure wannan dogon gashin nata cif a tsakiyar kanta,saita sake jelar tana lilo. Takalmin qafarta wani tsadadden boot ne da tayi cinikinsa da Europe ba dolla ba takanas ta saka aka kawo mata shi. Komai na jikinta fari ne qal,kamar yadda kalar thunder (dokinta) ya kasance fari tas.......me wani irin cikar zati da ban sha'awa ga duk mutumin daya kalleshi. Koda bakasan doki ba.......bakasan kuma darajarsa ba idan ka kalli thunder sai ya baka sha'awa qwarai. Qosashe kuma ingarman dokin data sayeshi daga United arab Emirates wato dubai da kudade masu nauyin gaske. Kulawa ta musamman take bawa dukkan dawakanta da kuma me duba lafiyarsu na daban data ajiye a Niamey da agadez. Akwai me musu regular check up da vaccination don tabbatar da lafiyarsu,hakanan abinsu na dabanne bayan abincin ana ciyar dasu fresh fruits da vegetables irinsu apple da carrots da sauran kayan marmari. Hatta da SULTANE yana sha'awar dokunanta......wani irin qauna ce tsakaninta dasu. A shekarun baya kafin ta zama busy akan kamfaninta har haka akwai ranaku na musamman da take warewa kawai don hawa ko zaman kallonsu ko lura da lafiyarsu. "Amma dai.......ki rufa mana asiri kada kallon tseren doki ya koma kallon biftu....." Wani murmushi ta saki sanda take dauko wasu safar hannu guda biyu. Sai data fara zurawa sannan fa daga kyawawan idanunta da kwallin data zizara musu a yay ya qara musu kyau. "Jikar muhammad agg nake......diyar muhammad hammud......akhnan.....biftu......don kawai na na shiga gasar tseren doki sai kuma jikina ya zama me abun banza ga kowanne kare da doki?......arahata batakai har haka ba" Ta qarasa fada tana zama saman wata ottoman sofa tana daidaita riding globes dinta cikin hannunta. Murmushi aisa ta saki,akwai abu guda dake burgeta game da akhnan din......tana martaba jikinta.......tana tsananin kula da qaunar jikinta,tana bashi kima da daraja,amma kuma wani abun na daban.....wannan izzar ta akhnan tana burgeta......wannan izzar ta akhnan tana saka mata shakku.......anya kuwa ba da gaske bane kuwa?,anya a yadda izzarta da alfaharin kanta yake zata iya auren wani d'a namiji bare wataran ya ganta gayarta?,bare wataran su hada gado kamar yadda tasha fada?......anya kuwa akwai wanda zai samu nasarar sauke wannan izzar?,anya kuwa akwai wani qarfi na wata aba soyayya da zai sauke wannan ALFAHARIN?.....ya cillata duniyar matsananciyar soyayya da shauqi?. Da wanann tunanin da yabar murmushi saman fuskarta ya kaita nisan da har akhnan din ta gama qarasawa shiryawa hankalinta bai kai ba. "Ma sha Allah" Aisa ta furta can qasan ranta tana duban akhnan din. Wannan skinny trouser din daya bayyana shape dinta......ta batar da wannan surar tata ta hanyar dora wata irin riga me kama da alkyabba maras nauyi sam sam,sosai ta baje daga bayanta ta kuma rage fitar da shape dinta yayi kwata kwata,rigar tana hade da hula ne wadda zata aza saman Egyptian turban cap din kanta me azabar kyau da aka qawata da adon gold stones. Daga gaban rigar me kaman alkyabba akwai wata 'yar lanqwasa da aka yiwa ado da wani tattausan gashi tun daga fuskar hular dake saman kanta,ya sauko saman qirjinta ya rufe tudunsu daga sama,duk da hakan bai boye shape dinta ba....sannan ta dauki helmet dinta ta riqe a hannunta. (08187255862 lu'u lu'u paying) Fadin irin kyan da tayi bata baki ne.......abu daya aisa ta sake tabbatarwa shine,da gaske akhnan din ta dabance......da gaske kuma tasha banbam da mata masu yawan gaske. Wani irin cika gurin yayi wanda bai taba yin irinsa ba,su kansu masu saida ticket na shiga gurin.....jami'an tsaro da kuma masu kula da kai kawon jama'a a gurin yawan ya rikitasu. Mafi yawan mutanen da sukazo kallon wasan sunzo ne don PRINCESSES AKHNAN MUHAMMAD HAMMUD.......don fiye da rabinsu basu santa ba sani na ido da ido. Sunanta ba boyayye bane cikin nijer dama agazed gaba daya......amma sanin anihin fuskarta abune da ba kowa ne zaice maka ga kamanninta ba. Kusan ita daya ta rage bata iso gurin ba cikin jerin 'yan wasan dake wajen......farin dokin qwaya daya dake tsaye ba maishi a kansa shima ya zama abu na daban daya tsonewa 'yan kallo ido. Ko cikin abokan wasan nata babu wanda dokin bai burgeba,duk da gabadayansu suna saman wasu irin qosassun dawakai da suka sha bamban da wadanda aka saba gani. *ADDIS ABABA* _national intelligence and security service(NISS)_ *_Washegari_* Wani irin sabo da horo ya yiwa ruhinsa,tun daga sanda ilimi da hankali ya gama wadatarsa kawo yanzu. Duk daren duniya......duk inda qarfe uku na dare yayi muddin akwai cikakkiyar lafiya a tare dashi to yabar makwancinsa izuwa saman abun sallarsa.......a kowanne dare a kowanne guri,hakanan a kowanne yanayi. Daga sanda ya karanta ya kuma fahimci ma'anar ayar nan ta cikin suratus sajdah aya ta sha bakwai da Allah madaukakin sarki yake cewa (Jukkunansu na nisanta da makwancinsu suna kiran ubangijinsu suna masu tsoron azabarsa.....suna kuma masu kwadayin rahamarsa......sannan suna ciyarwa daga abinda muka azurtasu). Tun daga wancan ranar zai wahala wani dare ya kubce masa ba tare da ya rayashi ba. Abinda yayi masa tasiri sosai cikin rayuwarsa......ba wata buqata da zai dorata saman abun sallar cikin irin wadannan dararen ba tare da yaga cikarta ba. Wani irin haske ne ke mamaye ruhi dama rayuwarsa gaba daya. Da gaske sallar dare na daga darajar bawa,ta sanya wani haske na musamman a ruhi zuciya dama fuskar me yinta,ga kuma tarin nishadi da walwala da zaka wayi gari cikinsa. Kiran sallar farko da wasu mintuna yabar saman abun sallar,ya koma bandaki ya sake sabunta alwalarsa don samun qarin haske akan haske(alwala haske ce......kuma itace ranar qiyama zata dinga zame mana tamkar fitila,itace kuma zata rarrabe tsakaninmu da kafirai,so yana da kyau ki zama me yawaita yin alwala ko zama da ita.....tana bada kariya daga dukkan sharrin me sharri). A nutse yasa dan qaramin lallausan towel dinsa dake fidda wani sirrintaccen qamshi daya samo asali daga turarukansa da yake amfani dasu ya goge lemar jikinsa,sannan yabi jikin nasa da wani sassanyan turarensa da mafi akasari shi yaf amfani dashi idan zai fita sallar asuba. (Turare kansa sunnah ce....sunnah me qarfi,cikin abinda aka sanyawa manzon Allah S A W sonsu akwai turare). Qarshen layinsu masallacin yake,kuma kusan shike jagorantar sallar asuba din a yawancin lokuta,duk da wasu lokutan yanayin aiki ma baya barinsa kwana a gidan bare ga samu yayi musu limanci. Cikin mintuna qalilan daddadar muryar nan tasa dake dauke da amon sautin karatu mafi daraja ya karade area din tasu,ya sake sanya nutsuwa sosai cikin zukatan duk wata halitta daka iya jiyo sautin nasa. Sanda ya kammala jagorantar sallar yaso ya zauna a gurin kaman yadda yakeyi wasu lokutan ya jira fitowar hantsi sannan yayi salatudduha(wata garabasa ce me girma ayin haka,gwaggwaban lada ne ga bawa me yawan gaske,ladan hajji da umra cikakkiyar lada cikakkiyar lada cikakkiyar lada haka annabi S A W ya maimaita har sau uku,idan bakije hajji ko umra ba.....ga dama ta samu a sauqaqe na samun ladaddakinsu daga gida)". Dole ya koma gida,don yana buqatar fita da wuri.....akwai abubuwan da yakeson dubawa kuma kafin ya isa headquarter dinsu. A nutse yake takawa zuwa gidan.......qasa qasa yana motsa harshensa cikin tasbihi ga ubangijin halitta. Sassanyar iskar asubar dake busawa tana sake dauke duk wani nauyi dake qirjinsa,tana saukar da wani nutsuwa da nishadi sosai a ransa. "Tsarki ya tabbata ga ubangiji" Ya fada qasan ransa,yana tuna yadda a alqur'ani ubangiji ke cewa a aya ta sha takwas cikin suratut takwiir "Da asuba idan tayi numfashi(ma'anar wannan sassanyar iskar me dadi dake kadawa tsakanin sallar asuba,ki gwada shaqarta,tana saukarwa da zuciya nishadi sosai)". "Ya akayi masu tsaronmu sukayi ganganci bar mana zakin qasarmu haka sasakai yana takawa zuwa gida haka gayansa?" Ya tsinci dattijuwar muryar daga bayansa. Tun bai juya ba qaramin murmushin nan nasa dake alamta nutsuwar dake jikinsa ya subuce masa. Koda bai juya ba yasan ba kowa bane sai alhaji muntassir amari. Dattijon da gidansa ke maqotaka da nasa ko nace yake kallon nasa. Dan asalin yankinsu garinsu na jimma,wannan hadakar garin ita ta kawo shaquwa da alaqa me qarfi tsakaninsa da alhja muntassir amari. Alhj muntassir tsohon ambassador din Ethiopia ne a Malaysia,wanda ya dauki shekaru masu yawa yana yiwa qasarshi hidima,bayan shekarunsa na retired sunyi ya dawo da zama cikin addis ababa da iyalinsa gaba daya. Yana da matar aure guda daya da yara biyar,uku mata biyu maza,ya aurar da yaransa uku,mata biyu namiji daya,yanzun 'ya'ya uku ne suka rage masa a gabansa. Menelik da dan uwanta yonas su kadai suka rage masa. Wani irin girmama haisam yake saboda abubuwa biyu. Na farko kasancewarsa d'a ga sarkinsu da suke matuqar so da bashi girma.......na biyu nutsuwa da tarin ilimin da haisam ke dashi. A aikace haisam din yaga alamu da abubuwa da yawa suka nuna yadda alhaji muntassir amari yakeson hada alaqa tsakanin haisam din da menelik.......menelik din da zuciyarta ta jima da narkewa haisam din......ta dade kuma tana addu'ar Allah ya kawo wani sanadi da alaqa zata qullu tsakaninta da haisam. Ta sani......ba wata hanya alaqa ko sanadin da hakan zata kasance,haisam din yayi mata tarin nisa......ya mata tazara me yawan gaske da take jin zata iya samun isa gareshi. Sam sam bashi cikin tsarinsa shiga shirgin mata,matan ma wadanda suke ba muharramansa ba irin menelik din. Yana da wani tarin kwarjini na musamman.......ya iya kuma iya tsare gida ta yadda zakayi tsammanin bai taba wani abu me kama da dariya ba. A wani dare da abbii dinta ya gayyato haisam din don yaci abincin dare dasu a mazauninsa na babban mutum na musamman a wajen mahaifinta. A ranar ta dauka tana da qwarin gwiwar iya tunkarar haisam ko yin wani motsi da zai bashi haske a kanta.......don ta wuni tana rehearsal na yadda zata shigo da yadda zata gaidashi,sai gashi a kallo guda daya tak da tayi masa ya rusa komai......ya ware wannan tsarin nata. Duk kuwa da cewa idanunsa da hankalinsa suna kan mahaifinta suna wata magana data shafesu amma sai yayi bala'in cika mata idanu harta nema daburcewa,ba kuma wai don ya daga idanu ya kalleta ko sau daya ba,hasalima idonsa nakan yonas dake gefenta yana amsa gaisuwarsu,duk da ya amsa musu cikin nuna mutuntawa da karramawa. Harta gama serving nasu komai ta juya zuwa ciki bai sake daga kanshi ko kallon sashen da take ba,don sosai ya bawa abbii dinta hankalinsa. Hankalinta ya tashi ya kuma kwanta duk a ranar,saboda bayan tafiyarsu taji abbii dinta yana gayawa ummiinta ma'anar gayyato haisam gidan. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 24 ____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ___________________________ "Menelik nakewa sha'awarsa........banason tayi asara kota rasa miji irin muhammad haisam din......duk da ina tsoron kada mutane suyimin mummunar fassara,su dauka saboda sarauta mulki ko tarin arziqinsu nakewa". Daga ranar sai hankalinta yadan kwanta,ta samu yaqinin a ranta,ta kuma samu tabbas tunda ga abbinta nan zai tayata wannan yaqin,yaqin da har yau ba wani ci gaba a cikinsa,saima sake nisa da haisam din kewa idanunta,don koda ganin gilmawar motocinsa ta samu gani a ranar daga corridor din upstairs dinsu,to lallai ranar ta shiga cikin jerin ranakun sa'arta. "To ya za'ayi?,barka da asuba" Haisam ya fadi yana bawa alhaji muntassir amari hannu sunayin musabaha. Tare suka jero bayan sun gama gaisawa suna dan tattaunawa kafin alhaji muntassir ya jefo maganar dake ransa. "Har yanzun dai kaqi sake amsa gayyatar cin abincin dare tare damu Muhammad?" Dan murmusawa yayi,wanda wannan karon kawai iya labbansa ne suka motsa. Yana jin nauyin yadda alhaji muntassir ke yawaita masa tayin zuwa cin abincin da a gurinsa baida ma'ana,ya rasa yadda zai masa bayani cikin girmamawa yadda zai gane. Ba zuwa cin abinci ko zuwa gidansa bane matsalar..... Matsalar tana ga yadda wancan karon ya bashi dama ya shiga har ainihin parlor din iyalinsa. A nashi tsarin bayan yayi aure........a duniya baiga wata qwaqwarar hujja da zaa bashi ba da zai sanya ya bawa wani baqo damar keta koda qofar farko ta gidansa wato gate dinsa ba har kuma ya kutsa zuwa ciki. Ko bayan haka ma shi abun bai burgeshi sam,uwa uba kuma ba wani sassauci ko hutu daya samu daga hukumarsu da zai samu lokacin zuwa ziyarar cin abinci,don haka ya hanke bashi uzurin qarshe kawai "Rashin lokaci ne kawai......ina fata kuma zaayi mana afuwa?". Murmushi alhaji muntassir ya saki,y fahimci bai iya wani boye boye ba,kai tsaye yakeyin maganarsa da dukka gaskiyarsa a yawancin lokuta. "Karka damu....qanwarka ke yawan tambaya dama,tana ganin kamar mun wareka,baka kusa da gida". Sai ya bashi hannu suka sake gaisawa ya taka a hankali zuwa qofarsa. A parlor dinsa yayi zamansa,zaman da kaman jira akeyi saqo ya shigo wayarsa,abinda kuma ya janye masa hankali kenan Tunda ya samu saqo daga abba muhammad dawuud da wasu taqaitattun kalmomin da su kadai suke gane ma'anarsu ya fahimci yanason ya rigashi isa office ne......na biyu yau ya tsara suyi zaman da zasu tattauna yadda tafiyarshi zata kasance......don haka yau din yana son yayi monitoring shige da ficen hukumar gaba daya bisa tsari na sirri yadda suka saba. A cikin ma'aikatansu waye ya shigo?,waye ya fita?,qarfe nawa ya shigo kuma qarfe nawa ya fita?. Tafiya ce me tarin muhimmanci ga hukumar tasu,saboda kasancewarta wani tsohon case da aka dauki shekaru ba tare da gano hasken komai ba a kai sai yanzu. Yau hatta da omari raba tafiya sukayi. Ya gama komai nasa akan lokaci ba tare da sanin dukka hadimansa bama,don ko breakfast bai tsaya beruk shugaba cooks dinsa ya kammala shiryawa ba ya fice. Shi daya ya zai motar da yake jin fita yau a cikinta ya fice abinsa. Sai yake jinsa yau sakayau.......ba guards ba hadimai.......daga shi sai shi sai kuma qira'ar qur'anin daya kunna a motar yana bi sannu a hankali yana tuqi cikin cikakkiyar nutsuwa da matsakaicin gudu. Yadda yake bin karatun kawai zai gaya maka yadda qur'ani ya zauna a zuciyarsa da rayuwarsa. Mutane na shiga nishadi da wani irin shauqi a sanda suke sauraron waqoqi......nashi akasin hakanne......yana jin dukka wannan nishadin......wannan shauqin da wannan jin dadin a sanda sautin qur'ani ke shiga kunnuwansa. Yayi wani irin kyau cikin ire iren kayan da yafi amfani dasu a ranakun aiki irin wannan Kurta pyjamas da sukayi masa bala'in kyau. Tattausan yadin da akayi kayan dashi da yadda yanayinsu yake ya sanya yawa yawan shigarsa kenan a ranakun aiki. Shiga ce da ba za'a kirashi na qananun kaya ba,hakanan ba za'a kirashi da manyan kaya ba kai tsaye. Kamfani na musamman dake samar dashi daga qasar india yake saka order dinsu a duk sanda suka fidda sabon design. A nutse yaqaraso babbar qofa ta farko dake zagaye da katangun hukumar tsaron dake da wani irin matakan tsaro daka iya zama barazana ga dukkan wani maras gaskiya,su sake kuma bayyana girma kima da darajar da gurin yake dashi. Cikin mamaki kuma tsaye suka wangale masa babban gate din. Ganinsa yau shi daya tsurarsa yana tuqi kuma hankalinsa kwance. Da sassauqan murmushi akan fuskarsa ya daga musu hannu,jami'ai da masu gadin dake a wajen suketa qoqarin gaidashi. Sam yau baya buqatar komai da zai tsaidashi,aikin nan da zai karba yake ji har cikin b'argo da jininsa. Yana jin wani zaquwa da kuma son zama da abba muhammad dawud. Akwai tarin sirrika dake binne cikin zuciyarsa.......akwai abubuwa masu tarin yawa daya binne a ransa,yabarwa kansa da kansa shi daya. Cikin personal elevator nasu ya samu ya isa office dinsa. Ya murda handle din a hankali bakinsa yana motsawa da sallamar nan data zame masa jiki a duk inda zai shiga. Da maida qofar da sauke idanunsa saman agogon office din nasa gami da shaqar daddadar iskar dake kadawa da sassanyan turaren office din nasa duka lokaci guda ya yisu. Yanason yanayin office din.......saboda yana son qamshi. A rayuwa kyautar abu biyu a wajensa tana da matuqar muhimmanci......kyautar littafi da kuma kyautar turare. Zai iya cewa baya jin akwai wata rana da zai rabu da zain me masa shara gami da kula masa da office dinsa,domin kuwa yasan kowanne yanayi da tsari da yafiso office din nasa ya zamana akai. Jakarsa kadai ya ajjye,ya taka a hankali zuwa wani sashe na office din,wanda aka yiwa dan qwarya qwaryar kitchen dake dauke coffee maker cups masu wani irin nau'i da kala da zasu tabbatar maka shi din JININ SARAUTA NE daga qabilar OROMO na yankin JIMMA. Komai nasa classy ne.......me tsari tsada da kuma nutsuwa ne. Bai zauna ba sai daya cika wata butar shayi da coffee.....wadda tafi kama da zungureren jug,ya zari cups har biyu sannan ya qarasa saman kujerarsa da yake iya juyata ya kuma sarrafata a duk yanayin da yakeso. Ba wai zama yayi hakanan a kanta kai tsaye ba,sai daya karanta falaq nasi da qulhuwallahu hadi da ayatul kursiyyu,sannan ya qarasa a nutse ya zauna akai yana ambaton bismillah. Hakan wani sabo ne da ya yiwa kansa bisa koyarwar nanay. Duk abu da yake cikin jama'a irin wannan daya tafi ya barshi na wasu awanni ko kwanaki,muddin ya dawo sai ya ambaci sunan Allah a kansa,takance. "Kana da tarin baiwar da ba lallai kai kan hangota ba......kana da quruciya da qananun shekaru......ka taka wani matsayi ka kuma taka wani matakin da wani yayi shekaru masu yawa yana harsashen samu......sai kayi tunanin kowa ne irin hakan zata kasance ya dauke idanu daga kanka?.......wannan matakin dakai kake rainawa......wannan matsayin da kake ganinsa ba'a bakin komai ba.......yana can wala'alla ya hana wani bacci.......yana can wataqila ya hana wani sukuni". Ko sau daya bai taba kawo wannan hasashen a ransa ba......har sai da nagartacciya uwa irin nanay ta ankarar dashi,daga wannan ranar,daga wannan lokacin kuwa bai sake yarda ko sau daya ya sauka daga abinda ta dorashi akai ba. Wayoyinsa ya hada gaba daya ya kashe don yana son maida hankali sosai akan aikin nasa. Ya zare takalman qafarsa yabar tattausar socks din dake qafarsa ya zuba coffee dinsa ya kuma daidaita AC din dakin sannan ya kunnna system dinsa. Bai shiga ko ina ba sai daya binceta tsaf,ya kuma tabbatar da komai yana kan saiti da tsari sannan ya fara hada aikin da yakega ya kamata ya hadasu tsaf kafin barinsa addis ababa. Kafin ya kammala aikin daya daukeshi awanni biyu cur ya shanye coffee dinsa,har yana jin buqatar qari. Shan coffee wani abune dake cikin jinin mutanen Ethiopia,musamman mutanen yankin jimma qabilar oromo. Noman coffee sukeyi da gasken gasken cikin manya manyan gonakin da idan ka gani zakasha mamaki. Ba wani cikin qabilar oromo da yake zato gari zai waye,rana ta fito ta fadi ba tare da ya kurbi coffee ko sau daya ba,walau yaro ko babba,mace ko namiji. "Alhamdulillah" Ya furta yana relaxing bayansa jikin kujerar sannan ya lumshe idanunsa yana qarasa rufesu ruf yana jin gajiyar zamansa waje daya yadda take bin sassan jikinsa. A hankali zuciyarsa ta nemi daukan hankalinsa a dan zaman da yayi yana son bawa zuciyarsa da kwanyar tasa hutu ta soma lulashi duniyar tunani,cikin nasara ya bude idanun nasa a hankali yana mamakin yadda ba wanda ya nemeshi a awanni biyun,duk da dama idan yana irin wannan aikin yana barin sanarwa a reception kan kada wanda ya nemeshi ko ya dameshi,idan ya kammala zai sanar,sai ya miqe yayi taku biyu yana jawo wata mini printer da yake using da ita wajen fidda bayanai da hadasu a matsayin document. Sau uku yana gwada fidda bayanan amma taqi bashi hadin kai,sai ya fuzar da iska daga bakinsa,ya koma a nutse yana maida takalmansa qafarsa,ya dauki system din nasa sannan ya kunna wayoyinsa ya juya yana fita a office din. Yana buqatar bayanan as document,babban sirri ne da ya shafi hukumar,so bazai iya bawa wani ya hada masa kundin ba,wannan ta tilasta masa fitowa da kanshi.. Dole ya duba wani department din dake da tsaro ya samu inda zai fidda files din. Yayi mamakin yadda shurun ma'aikatar ya yawaita,duk da yana ankare da kowanne motsi daga kowanne sashe,amma sanda yayi nisa a aikin sa sai ya turawa sashen kula da cameras ba kamfanin yace su nadad nad'ar masa kowanne motsi tsakanin mintuna da dukka awanni kowanne department zaiyi nazari akai. "AKHANAN MUHAMMAD HAMMUD.........AKHANAN MUHAMMAD HAMMUD.. . ....the princess of agadez" Wannan jimlar ita daya yaji ta maimaituwa daga inda bututun amsa kuwwar da ake kallon da ita. Baisan dane suke kallon ba zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 25 ___________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki __________________________ "Kai........dama da gaske akwai yarinyar nan ba labari bane cikin rubuce rubucen media?" Yaji muryar salana daya daga cikin jami'ansu yana fada da wani irin sauti da excitement. "Gashinan sun fadi sunanta.......da alama kuma fadin rai zatayi yarinyar......har yanzu taqi fitowa sai dokinta data gabatar,duk ya kashe idon kowa a wajen" Ya sake ji barrak ya fadi. "Yadda dokinnan yayi kyau na tabbatar kyakkyawa ce itama.......na qagu na ganta wallahi" Semere ya fadi. Samere din irin mazannan ne mash idanun kalle kalle da shegen son mata,wannan dabi'ar nashi ya sanya sam kanwarsa da suhaim basa jiquwa guri daya. Mugun shakkar suhaim din yake saboda kwarjinin da yake masa,yayin da suhaim din ba kasafai ya fiya shiga shirginsa ba. "Kamar gata nan.......gata can daga right side tana fitowa". Muryar data bashi mamaki,muryar omari ce......ko mene ya kawo omari cikinsu?. Yasan halinsa sarai ba irin shirginnan shima yake shiga ba.......amma tunda yaji anyi batun doki akwai alaqa me qarfi tsakaninsa da wasan dukka daya shafi doki,ba kuma omari din kawai ba......dukkan 'yan team dinsu ma. Wani abune da suka wareshi ya zame musu abu na nishadi a rayuwarsu cikin wasannin nishadi na halal. Wasan tseren doki,don kuwa halastaccen wasa ne tun zamanin ma'aki,don haka suka maidashi shima wasansu da sukanyi duk qarshen wata ko sati. Kowannensu gwani ne kuma qwararre,saidai a tarihin tafitar kaf haisam ne kawai ba'a taba cinyeshi ko fiddashi ba. Sau tari sukan zolayeshi da cewa. "Masu abu da abinsu ne.......kukam tun kuna jarirai aka tabbatar ana koyawa yaro komai daya shafi sarauta a masarautar jimma" Murmushin nan nasa dake cakude da wata charisma yake saki kawai. Duk wani abu da zai nuna martaba da girmansa ko ya tuna masa shi din wai wani ne daban da yasha banbam da sauran mutane bai fiya so ba,yafiso kullum su barshi ya dinga jin kansa kamar kowanne mutum......su daina tuna masa shi din dan sarauta ne. "Itace......wallahi itace" Daidai sanda semere yake fadin haka yana kasa daidaita zamansa saman kujerar da yake kai suhaim ya murza handle ya bude qofar yana shiga da sallama a bakinsa cikin husky voice dinnan nasa daya qara wani zurfi da fidda nutsuwarsa. Idanunsa na akan inda zai lalubo Omari,ya tuhumeshi da idanunsa akan dalilinsa na zuwa ya zauna a shirmen gurinnan bayan aikin dake gabansu?,cikin sa'a sai ya samu Omari din yana can gefe yana hada wata folder,abinda ya alamta masa akwai aikin daya shigo dashi office din kenan kamar yadda shima dalili ne ya shigo dashi. Hadiye maganarsa yayi,cikin ransa yana furta. "Subhanallah" Tare da sake imani da yaqini ga Allah. Tabbas shi yasa ubangiji ya jaddada muhimmancin yin bincike akan komai. Shigowar tasa ya sanya kowa a cikinsu miqewa cikin girmamawa suna kai masa gaisuwa tare da shan jinin jikinsu. Somawa motsawa kowa yayi don barin office din,don doka ne hakan a garesu,sai idan shi ya basu izinin ci gaba da zama. Ya fahimci wannan sak din da sukayi a yanayinsu,sai kawai ya basar yana amsa gaisuwar tasu,ya kuma doshi fannin da printers dinsu ke ajiye zai soma operating,salana ya dan matso. "Sir.......me kake buqata?" "Kebantaccen aiki ne" Ya fada a nutse yana daga masa hannu. Ya Fahimci yaren don haka ya koma mazauninsa,ya kuma dauki remote cikin dabara ya rage sautin tv din. Ba kasafai a guri irin wannan kowa ke nuna zurfin alaqa tsakaninsa da wani ba saboda dalilai na tsaro,kamar hakan ce tsakaninsa da omari. Girma yake bashi kaman kowa,duk da ana ganinsu sau tari da omari din fiye da kowa a cikin ma'aikatar,don haka bayan gaisuwa basuce da juna komai ba. A tsaye yake kyam yana aikinsa,dukka hankalinsa yana kan aikin ganin kowanne page ya fita daidai. A sannan dukka hankalinsu yana kan zazzafan wasan da ake kaftawa cikin birnin Niamey dake qasar agadez,wanda gidan TV na wasanni ta qasar yake daukoshi live tana watsashi a sassan duniya gaba daya. "Ya salam" Semere ya fadi yana rasa inda zai saka kanshi. "Kai subhanallahi" "An tashi kaina!" "Da gaske sarauniyar ce......ko a gudunta ma akwai izza da mulki a ciki" Wadannan dama ire iren maganganun nan su suke tashi cikin dakin cikin sauti na can qasa saboda wanzuwar haisam din a ciki. Suna zaton baya jinsu ko bazai jisu ba,saidai wani mugun kaifin ji Allah yayi masa tamkar dan maciji. Yana ji amma yayi kamar baiji ba.......yana gani sau tari amma yayi kamar bai gani ba......saboda qoqarin koyi da fadin ma'aiki YANA DAGA CIKIN KYAWUN MUSULUNCIN MUTUM.........YABAR ABUNDA BABU RUWANSA. Musamman idan abunnan bai shafi hani ko umarni ba akan wani abu daya zaman sabawa mahalicci ne. Ya soma gajiya da jin soki burutsunsu da maganganunsu,don haka yaja kujera ya zauna yana sauke boyayyen numfashi. Zuciyarsa yaketa kaiwa nesa,baya so yace musu komai,don ba a kowanne muhalli da kowanne guri yake magana ba,kowacce magana tana da tata gurbin da muhallin a wajensa. "Na jima banga wasan dokin da ya burgeni irin wannan ba" Omari daya bar abinda yake ya dawo cikinsu yaja kujera ya zauna ya fadi. Duk yadda yaso wasan kada yaja hankalinsa ya gagara yin hakan,wani irin wasa ne daya dauki hankula da idanun duniya. Zazzafan wasan da aka dauki dogon lokaci ba'a ga irinsa ba,saboda wanzuwar kallabi tsakanin rawunan dake cikin wasan wato AKHANAN MUHAMMAD HAMMUD sarauniyar yankin agadez. Futar "innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Da kuma "Subhanallah" Daga bakin omari kusan lokaci daya shine abinda ya fusgi hankalin haisam da hannuwansa ke saman shafukan takardar daya fitar ba tare da ya shirya ba. Kalmomi ne masu girma da nauyi a zuciyar kowanne musulmi,ya juya a hankali yana aza idanunsa kan allon television din,karon farko kenan da yayi hakan tun shigowarsa office din. Faffada kuma yalwataccen filin wasan dokunan ya fara yi masa maraba. Tarin ingarman dawakan da suka dauki idanunsa daketa qoqarin tserewa junansu suda mahayansu......suke kuma yunqurin kamo wani qosashen farin doki qal daya kusa isa iyakar da zata tabbatar da nasararsa. Ba'a zaune take saman dokin ba,ta miqe ne gami da duqawa kaman me shirin ruku'un riqe da linzamin dokin da wani irin zafi da yanayin dake nuna a yunwace take da isa ga nasararta don tserewa mafarautan mazan dake bayanta. Qarfin iskar dake ketasu ce ke dage alkyabbar dake jikinta,wannan ya bawa shape dinta dama skinny jeans din jikinta daya lafe a jikinta damar bayyana ta gefe da gefe. Da sauri ya dauke idanunsa yayi qasa dasu yana furta "Astagfirullah......astagfirullah" Wani bacin rai ya sauko masa,sai ya miqa hannu a zafafe ya kashe printer din ya kuma kwashe takardunsa yaja wani qaqqarfan tsakin da yaja hankalinsu. Dukkaninsu suka bishi da kallo yadda yake fita a office din a zafafe,kafin ihun da semere ya saki duka ta maida hankalinsu ga tv din. Baiyi nisa da wajen ba sautin muryoyinsu ya biyoshi har inda yake takawa don ficewa daga block din. Ihun daya tabbatar masa suna taya gwanar tasu murnar samun nasara daga dukkan alamu. Shi kadai yasake sauke ajiyar zuciya. Sam baiga alfanu ko dalilin da zai sanya mace irin wannan wasan ba. Idan har ta fito ne daga gidan sarautar da suke girmama addini da al'ada.......hawa dokin mace me haramun bane,ba kuma abu bane me muni,saidai yana da qa'idojin daya kamata a kula dasu. Qaramin tsaki yaja a ransa yana kuma ture maganar daga ransa. A yanzun akwai abubuwa masu yawa da suka fi wannan shirmen muhimmanci da suke a gabansa,sai ya miqa hannu ya dauki wayarsa wadda ya samu miscal din nanay har guda hudu. "Subhanallah" Ya fada yana komawa a hankali saman kujerar ya zauna yana qoqarin maida kiran. Tun safe yaso ya kirata kamar yadda ya saba......amma tashi da yayi da ayyukan yau a ransa yasa bai samu chance ba. *DAIDAI WANNAN LOKACIN* *_AGADEZ SULTANE MUHAMMAD HAMMUD PALACE_* "Lokaci tamkar takobi yake,idan kai baka yankeshi ba shi zai yankeka......kamar yadda lokaci baya jira........bai kamata muma mu jirashi ba........dogon jira wani lokacin kuskure ne......ganganci ne.......kuma wasa da dama ne........a wannan zamanin......a wannan qarnin TAMIM inajin cewa nakai iyaka......haquri na kuma yazo gaba.......kwadayina da buqatata akan taskokinnan sunzo iyakar da bazan iya juresu ba" Ta fada tana sake sarqe hannayensh da goyesu guri daya a bayanta,tana kuma takawa d'ai d'ai gami da zurfafa idanunta cikin na tamim dake zube qasa a gabanta. Murmushin dake can binne cikin qasan zuciyarsa ya saki,saidai ko fuskarsa bata bayyana hakan ba. "Akwai sauran lokaci.......gaggauta gabatar da komai zai iya tarwatsa komai din......" "Tamim!" Mammina ta kirashi a tsawace tana sauke hannayenta daga goyasun da tayi. "Kalleni da kyau!" Ta sake fada a kausashe tana fidda dukka idanunta waje kamar wadda ke buqatar ganin wani abu tarwai wanda bata samun damar ganinsa da kyau. Jajayen idanunsa dake da girman gaske ya daga yana zubesu a kanta kamar yadda ta buqata. "Kasan shekaruna nawa a duniya?" Ta sake fada nata idanun cikin nasa itama. Shuru na sakanni yayi,sannan ya girgiza kansa. "Shekara uku kacal na bawa sultane a duniya......shekara uku kacal......shin kwana nawa suka ragemin ne a duniyar........idan wadannan taskokin.......wannan mafarkan........wannan rayuwar idan basu iso hannuna ba sai yaushe?......zasuci gaba da zama a can?......zasuci gaba da zama a hannunsu suci gaba da narkewa?......wannan tabbaci kake dashi akan MOOTI?" Ta fada da zafinta sosai tana nuna hanya kamar a nan din komai zai bayyana a gareta yadda takeso. Wani gardin numfashi tamim ya fitar,sannan ya koma ya zauna sasai saman kilishin yana kuma sakewa.......tamkar ba shine wannan tamim din dake d'ari d'ari ba da iyakance muhallan da zai zauna ba. Yatsunsa biyu ya daga yana kallonsu kafin ya maida dubansa gareta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 26 ____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ "Iya wannan tazarar dake tsakanin yatsuna guda biyu......iya wannan tazarar ce kadai ta rage mana da shigarmu qasar......cikin wannan yankin kowanne dare mafarkina yake tuqewa......cikin wannan burin kullum tunanina yake saraya......tunanina yake narkewa......idan nace......" "Allah ya taimakeki!" Sautin muryar tafisu daga bayan hijabi ta ratsa zaren kowanne magana dake tsakaninta da tamim. A fusace ta waiwaya,saidai hankalinta a kwance yake. Hijabin data sanya daga kowanne idanu da zai iya ganin wanzuwarta a wajen ita da tamim......kamar yadda tafisun bata isa ta qara koda taku guda daga inda take tsayen ba. Uwa uba tafisun amintacciyarta ce.....kalar amintacciyar da ba irinta kaf cikin hadimanta,saidai kuma kowanne mutum tana tsaidashi a matsayinsa......a gurbinsa......a kuma matakinsa. Sai data numfasa na tsahon wasu mintuna sannan ta daidaita muryarta da kanta. "Ya akayi?". " Maude ne yazo da wani saqo,yakeso ya gabatar miki dashi" Yalwa ta fada girmame. Maude din yana daga cikin mutanenta na amana......kamar yadda ta tabbatar tunda tafisu ta tsallako har nan nemanta ba shakka abune me muhimmanci ya taso. Bata amsawa tafisu ba,tadai juya ta yiwa tamim kallon da yake gaya masa ta jirata,ta juya da takun mulkinta tana nufar qofar fita. Idanu ta zubewa maude bayan ta zauna,baice komai ba ya matso yana miqa mata wayarsa. Tafisu ce ta matso tana karbar wayar daga hannunsa sannan ta qarasa da ita fuskar mammina. Kallon mintina goma ta yiwa wayar......tana dab da cewa tafisu ta janye wayar sunan akhnan ya bayyana a jikin dokinta sanda take zabga gudu kamar bata tsoro ko hasashen abinda zai iya faruwa da ita idan ta fadi "Me nake gani wannan?" Mammina din ta furta tana janye dubanta daga fuskar wayar,tana kuma hade girarta sosai tana son dora yanayin saman fuskarta yadda zai dace da fuskartata. Can qasan ranta kuma wani abu yana motsawa,wasu tarin abubuwa suka fara motsawa sannu a hankali. Qasa maude yayi da kansa cikin tsananin ladabi. "Ki gafarceni.....kiyimin afuwa........gimbiya akhnan ce,cikin gasar tseren dokuna ta yankin Niamey" "Gasar tseren dokuna?" Ta fada cikin mamaki tana duban maude. Sake qasa yayi da kansa. "Tabbas.....kiymin afuwa Allah ya baki yawan rai........na durfafeki da maganar ne saboda na tabbatar abune dake ba zakiso ba.......banason kuma ace me martaba yaji wannan maganar......na tabbatar zaki tsawatar zaki kuma yiwa tufkar hanci don lamari ne da bai dace da al'adunmu ba" Shuru kawai tayi tana juya maganar cikin ranta. Ma'aunai guda biyu ta aza maganar maude......ma'aunai masu nauyi da kuma zurfi tanason gane a wanne ma'auni ya kamata ta dora maganar. Shuru ne yaci gaba da wanzuwa cikin parlor din. Tsahon wasu daqiqu,a hankali ta sauke wani boyayyen numfashi daya fito da wani sirrintaccen murmushi daga fuskarta. Duk da ba'a yanyin murmushin take ba......hasalima ba lokaci bane daya dace da fitar hakan saman fuskarta ba.....amma gilmawa da haskawar wani tunani cikin kanta ya sanya dole murmushin ya qwace mata. Yatsunta ta murza guda biyu wanda suka bawa maude hasken abinda take nufi,don haka ya sake rusunaw yana fadin. "Na barki lafiya". Har yakai bakin qofa ta kira sunansa cikin izza. "Maude" "Allah shi baki yawan rai". "Bana buqatar komai.....bana buqatar kowanne motsi......idan da wani buqata zan magantu". "Yadda kikeso haka za'aci gaba dayi.......ba'a gidan bama.....a qasar agadez gaba daya" Ya furta da wani salo daya sake sanyata jin qarfin nata girman yana sake ninkuwa. "Kiramin biftu ki bani ita" Ta sake cewa da yalwa ba tare data kalli yalwar ba. A ladabce ta miqe ta taka da hanzari ta fita. Ba jimawa ta dawo da wayar ta budeta ta kuma kira layin akhnan din kai tsaye. Su uku ne kacal cikin motar banda motoci biyu a gaba da bayanta suke musu rakiya daga filin wasan zuwa gida. Wani irin nishadi takeji a zuciyarta,kalar nishadin data jima bata samu irinsa ba. Sosai takejin walwala,tana jin wani alfahari da kanta yana saukar mata. Babban abinda yake qara ninka farincikinta........maza guda goma sha daya data yiwa zarra ta kuma zubdasu a filin........ta zame musu kallabi tsakanin rawuna. A cikin qwayar idanunsu taga zafin hakan,a cikin motsinsu ta hangi daci da bacin ran da sukaji game da hakan......hakan takeso........shine buri da muradinta. Ta bata ran kowanne namiji da yakejin yakai.......tabar masa tabo da ciwo me taba zuciya a matsayinta na diya mace. Dukkansu qwararrun 'yan wasa ne da akeji dasu cikin Niamey,tasha kallon wasansu,kusan kowanne a cikinsu tana da record dinsa....mayun wasa ne da ake matuqar ji dasua Niamey din da kewayenta.......sai gashi a yau bugun farko dukka ta zubdasu. Daga nan inda take tana iya jiyo yadda ake kiran sunanta ta amsa kuwa. Lambobin yabo da na girmamawa......shaidar lashe gasar dukkaninsu ta watsar bata tsaya saurara ba bare ta karba ta taho abinta. (08187255862 for lu'u lu'u payment) Tasan akwai tarin daruruwan mutanen da suke son daukar hoto tare da ita. A wajenta wannan din duka shirmene,bata shirya bawa kowa dama yazo kusa da ita ba,uwa uba ita ba wani lambar yabo tazo karba kona girmamawa ba. Girma dashi dama suka ganta,yabo kuwa iya na bakin mammina da sultane sun isheta. Ta shiga gasar ne kawai don rad'in kanta,ta shiga ne kawai don farincikinta,ta kuma shiga ne don haka takeso haka kuma take sha'awa. Cikin Lamborghini din da tazo musamman saboda daukarta suke ta barsu da kururuwar kiran sunanta. Ita da aisa sai shehnaz. A nutse take cire helmet din kanta ta miqawa birran. Karba tayi sannan ta matso tana zare mata boot din qafarta. Barratu ta miqa mata tataccen ruwan cranberry juice me matsaikaicin sanyin da bazai cutar da haqora ba. "Biftu wannan wasan bai cika ba......Vouse avez fait un mauvais choix(kinyi yanke hukunci mara kyau),IIs te réclament toujours au micro(har yanzu kiranki sukeyi ta mic)". Ajjiye cup din tayi a saman tafi hannun birra dake duqe gabanta tana jira ta gama,ta karba cup din ta matsa can wajen wani madanni daban dake jikin motar ta latsashi tana maida komai saman dan tray din daya fito. Lallausan handkerchief dinta ta sanya yana goge dogayen yatsunta farare sol da babu digon komai koda saman farcenta,daidai sannan aisa itama ta tanka. "Ki gaya mata dai.......wannan wasan bai kamata ya tafi a banza ba........Tu as joué un bon match(kin buga wasa me kyau.....ni kaina nayi mamaki". Shigowar kira wayarta da number mammina yaja hankalinta fiye da qorafinsu,sai kawai ta yiwa birra alamu,da hanzari ta ciro mata Bluetooth dinta ta miqa mata ta maqala a kunnenta tana relaxing sosai cikin kujerar "Ba abinda ya kaini kenan ba......ba yabo nake buqata ba bare na karbi nombre(number).....me so a cikin ku tana iya komawa ta karba daga baya" Ta qarasa maganar tana daidaita Bluetooth din a kunnenta cike da dokin son yin magana da mammina din da take jin kewarta har zuciyarta. Aisa ce ta watsa mata harara tana dora qafarta daya saman daya. "Eh ga gantalallu ba". Bata ma ji abinda take cewa ba saboda hankalinta ya tafi ga wayar. "Bonjour mammina" Ta fada a shagwabe kaman yadda ta saba yin waya da ita. A duk sanda take gaban mammina......ko take waya da ita,tana jin kanta kamar qaramar yarinya. Wani girma da izza takeji sosai a duk sanda take tare da mammina din. Itace mutum ta farko data dasa sarauta da kuma izza sosai a tattare da ita......ta sanar da ita wacece ita a aikace......ta sanadin mammina tasan irin daukakar da Allah ya bata. Nisan tazara da banbancin dake tsakaninta da sauran yaran masarautar dama qasar agadez gaba daya. "Me kikayi haka AKHNAN?". taji saukar tambayar daga bakin mammina ba tare da tabi takan welcoming nata da tayi ba. Gabanta ya fadi......saboda taqi jinin dukka wani abu da zata yiwa mammina din har ya kawo motsuwar ranta ko rashin jin dadi a tattaare da ita,harma kuma hakan ya nuna ga fuskarta. "Kinason ki manta ke wacece akhnan?.......kinaso ki manta tsada da darajarki?.......me kaiki shiga tseren doki?.......har kina yin kamar zaki fadi bayan kinsan tsada da darajarki?......bakisan kin wuce ajin irin wadannan abubuwan ba?......me kike nema?". Boyayyar ajiyar zuciya ta saki kafin ta narke murya,har cikin ranta tana jin ba dadi da yadda tasa ran mammina din ya baci har taji ba dadi har irin haka a kanta. "S'il vouse plaît mammina.......nayi hakanne kawai don nishadi na fa?" Ta fadi kaman zata saka kuka. Ta fadi da wannan narkakkiyar shagwabar da mammina din da kuma sultane kadai takejin kanta a hakan a gabansu.......batasan ko akwai wata halitta a doron qasa data cancanci wannan zubin yanayin da kuma tsarin ba. "Amma idan sultane ya gani yace me?,kina zaton ranshi zaiyi dadi?". "Excusez-moi(sorry)mammina........Je suis vraiment désolé(am really sorry),don Allah karki fadawa sultane mana mammina". Shuru mammina din tayi,kaman ba zata sake cewa komai ba kafin tace. "Shikenan,kada hakan ya qara faruwa" "Je ferai preuve de diligence(zanyi qoqarin hakan sosai)" Ta amsawa mammina tana sauke boyayyar ajiyar zuciya na samun sukuni. "Kika ce?" "Mammina zanyi qoqari sosai akan hakannnn" Ta sake fada kama zata saki kuka,saita dora da "Salut......À plus tard(sai anjima)" Tana dan boye sirrintaccen murmushin nan nata. A nutse ta yiwa yalwa alamun ta gimtse kiran. Cikin cika umarni yalwa din ta janye kiran ta kashe kiran ta dora wayar daga saman wani tattausan tuntum. "Murmushi.......kulawa......nuna qauna.......damuwa da dukkan lamurannan.......bansan daga ina kike iya zaqulosu daya bayan daya ba" Muryar yalwa ta maye gurbin shirun da parlor din ya dauka,kafin a hankali yalwan ta waiwayo tana zube idanunta cikin na mammina,kamar ba itace a dazun kanta yake qasa da inuwar mammina din ba. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 27 ____________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ Itama nata shimfidaddun idanuwan mammina ta zubawa yalwa. Kamar masu gasar tantace qurewa juna kallo. Tsahon wasu qayyadaddun sakanni,mammina ta miqe a hankali ta soma takawa. "Bansan daga ina suke tahowa ba......bansan daga inda suke gina kansu kuma su bayyana a maganata da fuskata ba......abu guda daya na sani......mutuwa kawai nakeyi yalwa a kowanne bullowar rana da faduwarta......mutuwa nakeyi ina kuma sake mutuwa tsahon shekaru ashirin dinnan.......ki aika saqo zuwa ga *SAHEL COUTURE* Na Niamey........lokaci yayi da kowa zai motsa........inason kowanne dan makunni ya kunna kansa.......ina buqatar kowanne gini ya motsa......ina buqatar kayan aiki su wasa kansa.......su kuma fara abinda aka haliccesu saboda shi!" Ta qarasa msganar daidai sanda ta isa qofar da zata fiddata daga parlor din. "Ayi musu bita......ayi musu tilawa.....sannan kuma a maimaita musu......dukkan kuskure qwaya daya tal......daidai yake da bugun numfashin zuwa guda daya.......dukkan sakaci guda daya kuwa.......daidai yake da rage adadin yawan fitar numfashi da maidashi zuwa ga mashaqa iska" "An gama ranki ya dade" Yalwa ta fada da wani irin biyayya me zurfi tana sauke kanta qasa,wutar dake ci a tata zuciyar tana soma rura kanta. Cikin izzarta ta isa inda ta tashi dazun idanunta akan tamim da wani irin nazartaccen kallo. "Me kake fadi dazu?" Ta jefa masa tambayar da yanayi na izgili. Sautin daya tabbatar masa ya fadi wani abu ba daidai ba.......ya fadi wani abu da bai dace da ra'ayinta ba.......bai kuma dace da abinda takeso taji ba. Saidai a ransa yana jin dole ya maimaita mata......don baya fatan ta jawo wani kuskure da zai zama almakashin gintse jira da haqurinsu na shekaru kusan GOMA!. "Ba wani gurbi da sauri yake dashi a!" "Tamim!" Ta kirashi a zafafe tana sake jin cewa haqurinta da gaske yazo qarshe. "Kodai baka shirya ba?......" Ta masa tambayar me tarin ma'anoni da yawa. Dubanta kadan yayi,kafin murmushi ya subuce masa,ya danyi qasa da kansa kafin ya dagashi zuwa gareta. "Inda TAMIM ba shiryayyen bawa bane......na tabbatar a yanzun labarin shekaru goma da abubuwan da suka shude da ita a ciki BASHI AKE MAIMAITAWA A YANZU BA!". Ya fada yana cika idanunsa da yaqinin da yakeso ta cikashi a zuciyarta,ta kuma sanya hakan har can qasan ranta. Idanu ta kafeshi dashi sosai cikin salon nazarta da karantar mutum kamar yadda ta saba. A nutse saidai da wani irin sauti me tarin ma'anoni tace masa. "Wannan jarumtar.......wannna zarrar.......ita na gani......ita ta sakani zabarka na sakoka cikin wani sha kundum din sirri da ya shafi rayuwar zaituna gaba daya........zaituna bata jiran banza.......bata taba jiran wani abu a rayuwarta har haka ba.......dole ya wannan abun dake binne a tonoshi!.......dole wannan damar da muke ganin qyallinta take mana b'aton dabo ta ruskemu.......koda mu bamukai ga takawa izuwa muhallinta ba........har zuwa yaushe komai zai qare?!......ya kamata ya fahimta.......ya fahimci akwai mafarauta.......akwai masu tarin buqata.......ya kamata a sanyashi ya waiwaya.......ya kuma yiwa kansa da kansa karatun da bai buqatar me fassara!" "Biyan buqatarki itace muradina........amma har yanzu inason tuna miki cewa............ZAKI NE dake qarqashin kulawar DAMISA!!". Tamim yayi maganar kowacce gaba ta jikinsa tana motsawa. Kamar daukewar ruwan sama bayan shafewar dogon zango yana zuba haka shuru ya gifta a dakin. Sosai maganar ta daki zuciyar mammina da wani irin qarfi daya tilasta tsaiwar bugawar jini zuwa ga sassan jikinta na wasu qananun daqiqu. "Tamim......." Ta kira sunansa,saidai kafin takai ga cewa komai ya rigata dora maganarsa akai. "Za'ayi........za'ayi......za'ayi.....bansan meye zai dakatar dani daga qarasa wannan aikin ba!" "Haka nakeso naji!" Ta fada cikin wani qwarin gwiwa daya lullubeta gaba daya. "Ban miki alqawarin komai zai kasance kamar yadda ya kasance a baya ba......saboda komai din a yanzun ba yadda yake bane a baya!" "Na baka wannan amannar.......na kuma baka wannan yardar" Ta fada tana bude tafukan hannayanta kamar wadda kewa qasa daquwa. Idanunta a kansa har ya fice gaba daya. Dauke kallonta tayi tana qoqarin maida dukkan qwarin gwiwarta gangar jikinta.......taja wata sassanyar iska da garin ya fara saki sakamakon hadarin da ya kammala haduwa ya kuma hade jikinsa guri guda. Miqewa tayi ta fara takawa,tana jinta a wata sabuwar zaituna......wata sabuwar mammina......wata zaituna ta daban ba wadda take jinta a yanzu ba. ★K'arfe bakwai da rabi ne na dare a garin addis ababa dama Ethiopia gaba daya. A daidai wannan awannin wasu sirrintattun awanni ne da suka kammale abba muhammad dawud......omari.......da haisam guri guda cikin wani kebantaccen office dake da wani irin tsaro da sirri. Abba muhammad dawud din yana zaune ne cikin kujerarsa swivel chair,yana jinsa yana sake narkewa a cikinta saboda maganganun da suka kammala yi a yanzu. Daga can saman wasu swivel chair din omari ne.......wanda ya soke yatsunsa guda goma cikin na juna.......yana jin wani abu yana masa amsa kuwwa cikin kunnuwansa shima tun bayan daukewar kalamai daga bakin kowannensu. Haisam din,wanda ke zaune sosai saman wani table dake ajjiye musamman saboda karatu,a maimakon cikin kujerar,ya nannade hannun kurta pyjamas din jikinsa,yatsunsa dauke da biro yana kadashi a hankali,manyan idanunsa da suka lumshe kadan suna saman allon dake gabansu da suka gama rubuce rubuce mintuna kadan da suka rage. Daga muhammad dawud har omari hankulansu suna kan haisam ne. Omari cike yake da fatan yaji haisam yace ya janye zuwa NIGER ya janye shiga birnin AGADEZ. Tarin hadurran suna da yawa......tarin sharuddan sunyi nauyi da girman da yake ganin haquri da tafiyar yafi alkhairi. "Na shirya......zanje!" Haisam din ya shammaci ji da ganinsu dukka ya furta yana ajiye abun rubutun hannunsa,sannan yayi qaramin tsalle yana dira daga saman table din yana ware hannun kurta dinsa daya nade. Dukkansu idanu suka zuba masa,zallar mamakin qarfin halin haisam da jarumtarsa tana kad'a Muhammad dawud. Yanzun nan......da kansa ya sakeyin wadansu binciken........da kansa ya duba komai,ba wani bane ya duba ba......ba wani bane ya bincika ballantana yayi tunanin bai fahimci abun daidai ba ta sigar bayanin da sukayi masa. "Ka tabbatar ka shirya muhammad haisam?" Muhammad dawud ya fada a ransa yana fatan ko yaya ne haisam yace ya janye. Da wannan qasaitar tasa ya tako a hankali,ya qaraso gaban table din muhammad dawud,ya janyo kujera qwaya daya ya aje a gaban nasa sannan ya zauna. "Karanto komai kawai......ka karanto yadda komai zai kasance" Ya fada yana cire murfin biron dake hannunsa ya rufe biron ya ajiye gaban Muhammad hammud......abinda me gaya masa haisam din baida buqatar rubuta komai......kwanyarsa ta shiga yanayin da zai iya riqe komai da basirarsa kamar yadda ya saba a yawancin lokuttan da ya dauki abubuwa serious da gasken gaske. _TOFA_ ★★★★ Awa guda cur suka shafe suna tsarawa da tattaunawa gami da shirya yadda komai zai kasance kafin su kammala. Tsam ya miqe,ba wani rauni daya bayyana a gangar jikinsa bare kuzarinsa ko kadan,daya daga cikin abubuwan dake burge abba dawud kenan matuqa tattare da haisam din. Yasha fada yana kuma maimaitawa "Tabbas haisam halastaccen jinin abba jifar ne.......da gaske shi din sarauta cikin jininsa take......gado ce ta tun usul......irin wadda idan ta ratsa mutum take maidashi jarumi na gasken gasken. Jarumtarsa tafi kama da jarumtar kakanninsa da suka shude a yawancin lokuta,wadanda suka tsayawa qasar Ethiopia......tsaiwar data sanya aka gagara yi mata irin mulkin fyadiya da aka dinga yiwa qasashen africa a wancan lokacin. Hannu abba muhammad dawud ya miqawa omari dake tsaye a gefan haisam din yana sauke numfashi. Dariya ta kufcewa abba muhammad yana finciko omari din da shima dariyar ta qwace masa. "Omarul farouq fa kake........me wannan sunan jarumi ne da baisan tsoro ba ko kadan.......jarumtar data sanya hatta da shaidan baya iya hada hanya dashi ka manta?". Murmushi ya sake kubcewa omari yana girgiza kansa. "Muhammad ya fini jarumta......kuma ya fini son kasada da rayuwarsa......abba bakaji me yake fada ba?,so samu muje har niger a mota......me yayi zafi?,kawai don zuciyar dutse gareshi?" Ya qarashe maganar yana zube kallonsa akan haisam dake hada kayayyakinsa cikin wata jaka ta musamman. Baiko waiwayo ya kalli omari ba......saboda shi ko sau daya ko alama baiji wani fargaba ko shakka akan komai ba. Hankalinsa kwance yake,bayajin akwai abinda zai sanyashi ya janye. Ya sani......gagarumin abune shiga wata qasar ba tare da izinin qasar ba......shiga wata qasar da zummar aiwatar da aikin da ya shafi tsaro bincike da samo bayanai daga wasu ahalin qasar.......to amma hadarin dake fuskantarsa.......hadarin dake fuskantar masarautar jimma ya kere dukka wadancan hadurran a ransa. "Karka damu......na yadda da muhammad.......bani da tsoro ko fargaba a kansa.......amma nasan halinka.......indai baka yiwa mootii bayanin aikinnan da kyau ba ni da kaina zan masa.......don kada ka tafi ka barshi da tsammanin dawowa kwanaki kadan a nan kusa" Abba Muhammad ya fada yana qoqarin boye tashi fargabar. "Alfarma daya abba". Haisam ya fada yana goya backpack dinsa a baya gami da gyara zamanta. "Uhummmm.......fadi muhammad" Abban ya fadi yana dubansa. "Ba yadda zaa canzamin wannan b'eran?" Dariya taso kama muhammad dawud. Daga ganin idanun haisam da gaske yake fadi,ba tun yau ba ya sani,duk wani aiki da zai shiga ko zai jagoranta to ba shakka sai ya zabi mafiya nagarta wajen jarumta da qwarewa sannan yake aiwatar da aikin. "Kasan dokar aikin mu haisam.......indai kasan wani abu a ciki ko akai......to ka shiga cikin aikin ko ka shirya ko baka shirya ba". Muhammad dawud ya fada yana danne dariyarsa ganin kallon da haisam ke jifan omari dashi. Idanun nasa ya dauke daga kan omari din,ya fara takawa zuwa qofar fita daga office din,yayi scanning card dinsa qofar ta bude masa,ya saka qafarsa daya a waje sannan yayi magana ba tare daya waiwayo ba. "Kaja masa kunne.......ka sake karanta masa komai,bazan dauki sakaci ko ganganci ko wani tsoro ba.......mu ba mata bane......an haifemu don mu fita muyi farauta......an haifemu don mu zama garkuwa......bango majingina" Ya qarasa fada yana qarasa ficewa ya maida qofar. Sanda yake saukowa daga escalator yayi mamakin hango abdii sosai. Tsaye yake a lobby din shi daya,cikin shigar qananun kaya. Hannayensa zube a aljihun wandonsa yana duba wayarsa. "Abdi" Ya fada qasa qasa yana motsa labbansa idanunsa a kanshi. Baisan wanne irin qauna yaron yake masa ba......wannan qaunar ita ta sanya ya gutsira abdii kadan daga sirrinsa da ko nanay bata sani ba. Boyayyen murmushi ya saki da bai bayyana akan fuskarsa ba. Ya sani zai wahala abdii ya iya zama sai ranar daya tsara zai dawo din,ya tabbatar tunda ya taho shima hankalinsa yayo addis ababa,yanzun kuma da zai tuhumeshi me yasa ya yanke hutunsa tun yana da ragowar lokaci zaice wani uzuri ne ya taso daga makaranta. Kamar a jikinsa yaji haisam din yana wajen,sai ya daga idonsa a hankali ya sauke kan escalator din. Murmushi ya sakarwa haisam din yana maida wayarsa a aljihu,ya kuma matso a nutse bakin escalator din yana jiran qarasowarsa. "Saurin na meye abdii?" Haisam din ya furta a nutse yana dauke idanunsa daga kan wata mace dake shigowa gurin wadda kafatanin hankalinta da idonta yake kansa. Sumarshi ya shafa a hankali yana miqa hannu zai karba jakar wajen haisam din,wanda aiki ne na hadimansa da guards dinsa,wanda baisan me yasa wannan karon yake nesanta kanshi dasu ba. "Uzurine daga makaranta obbo" Ya fada yana shafa qeyarsa. Dole a wannan karon wannan murmushin dake da gurin ajiya na musamman ya subucewa fuskar haisam,yadan lumshe kyawawan idanunsa yana kuma budesu duka akan abdii. "Abdii......qaryafa tana cikin manyan zunubbai". "Obbo mana......ba qarya nayi ba.......uzuri daga makaranta,kai din makaranta ne obbo.....akwai uzurin da yafi wani ya kasance dakai?.....hankalin mooti yaqi kwanciya kaman yadda nawa ya kasa kwanciya......shine kawai mukayi shawara dashi na biyoka......daga nan har AGADEZ " Idanunsa masu nauyin nan ya zubawa abdii,har sai da abdii din ya gaza jure kallon nasa,yaja baya kadan yana cewa "Obbo.......your eyes obbo" Yadda yayi maganar da gaske kallon ya masa nauyi,sai haisam din ya janye idanun nasa ya soma takawa zuwa qofar da zata fiddashi daga gurin ba tare da yace da abdii komai ba. Qasan ransa yana juya yadda tafiya da abdii zata iya yiwuwa da kuma rashin yuwuwarta......duk da qiris ya rage abdii ya zama wani bangare na national intelligence agency a department dinsu. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 28 __________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ Driver dinsa da baisan sanda ya biyoshi ba shi ya bude masa qofar motar,ya shiga a nutse ya zauna yana sauke numfashi. Batun tafiyar da dukka maganganunsu shida muhammad dawud ke masa yawo,indai har zai gayawa mootii komai game da tafiyar......to bai kamata yabar nanay cikin duhu ba,yana jin ya kamata ko yaya ya haska mata,ya kuma buqaci addu'arta. Abdii keta masa hira yana saurarensa kawai. Bai gaza ba don yafi kowa karantar yanayin haisam din a mabanbantan lokuta. Ya sake kallon agogonsa,yana jin omari yaja lokaci da yawa bai fito ba,mutum ne shi bai baza uzuri sosai......bayason kiran omarin,bai sani ba ko suna magana me muhimmanci da muhammad dawud ba......amma ya gaji,gida yakeso ya qarasa ya samu ya bawa kwanyarsa hutu. Ya daga ido da zummar yin magana ya hango omari din,sai kawai ya gyara zamansa yana jiran isowarsa. Ko cikin mota shuru ya zabi yayi,don yayi doguwar maganar da shuru yafi buqata din a yanzu. Yawan magana ko doguwar magana wani abune da suke sanyawa yanzu yanzu qirjinsa ya fara zafi,ballantana kuma akai ga hayaniya,sam basa shirginsa. Sau tari idan suka hadu dukka dasu taarik,hira da rudu irin na abokai shikam nashi baya nisa. Ba yanzu ba,tun a makaranta sanda suke tsakanin shekaru goma sha biyar zuwa sama. Littafi kawai zai dauka yayi maka wannan dogon zango,ya jima yana karantashi ba tare daya gaji ba......hakanan qur'ani da zai jima zaune shi kadai a kebantaccen guri yana tilawa abinsa. Susan ya yanayi da dabi'arsa take,wannan ya sanya sau tari idan sukaga yayi shuru irin haka ko ya kebe kansa basu fiya damunsa ba. Ba jimawa suka isa kazanchis layout,unguwar dake cike da wata irin nutsuwa da kullum take qarawa haisam son zama a cikinta. "Mu sauka muyi sallah kafin mu.....shi ya qarasa gida da motar" Haisam ya furta. Dukkansu sun aminta da hakan,don ba wanda ba'a gajiye yake a cikinsu ba. A babban masallacin unguwar suka qarasa ciki bayan sunyi alwala,tuni har an daidaita sahu,saidai shigowarsa ya sanya limamin neman ja da baya don bawa haisam daman jan sallar. Hannu ya daga masa yana girgiza kai,don ba kasafai ya fiya son haka ba. Yanajin kamar an aza masa nauyi ne an kuma banbamtashi da sauran mutane. Basu jima ba suka baro masallacin. Tare suke takowa su ukun,duk da abdii ya danyi gaba dasu dasu kadan bai jera kafada dasu ba. "Haisam" Omari ya kirashi a hankali. "Na'am" Ya amsa masa,don dama tun dazun ya fahimci akwai maganar dake bakin omari din,yanayinsa daya gani na rashin son hayaniya ya hanashi cewa dashi komai. "Baka hango kowanne illa da hadarukan dake cikin aikinnan?......me zai hana ka haqura a aika wani?" Omari ya fadi da sigar dake nuna daga zuciyarsa maganar ta fito. Bai zabi ya amsawa omari da wuri ba,har sai bayan shudewar wasu sakanni. Tsaiwar da dakatawar da haisam yayi da tafiya shi ya sanya omari shima tsaiwa. Manyan zagayayyun idanunsa ya zube akan fuskar omari.......muryarsa d alamun gajiya sosai,gajiyar da bata hana jarumtarsa bayyana cikin muryar tasa ba yace. "Bana tunanin akwai wanda ya fini cancantar aikin nan........abu daya ka sani......ajani amintaccen mooti ne.......amma kasan cewa mooti ABUN FARAUTA NE?!" Da wani bahaguwar ma'ana maganar ta saukarwa omari a sanda baiyi zaton jinta ba,wannan ya sanyashi bude idanunsa sosai saman fuskar haisam yana kallonshi. Koda omari baice bai gane ba......koda omari baice qarin bayani yake nema ba.....amma iya kallonsa kadai da yakeyi ya fahimtar dashi hakan. "Eh.....ina nufin abinda na fada omari.....mooti abun farautarsu ne da suka gaza cimmasa........suna raye kosu waye suka aikata wannan aikin......jikina yana bani ba mission na mutum daya bane......ba kuma sashe daya bane yake farautar MOOTI.....kasan sau nawa a cikin shekaru goman nan na tare yunqurin kaiwa mooti hari ba tare dashi kansa ya sani ba?". Sake dukan omari maganar tayi......ta dakeshi da wani irin yanayi da har sai daya kamo hannun haisam. "Mooti kuma......meye hadin mooti da wannan case din har na tsahon shekaru goma?" "Abota da dangantakarsa da ajani" Haisam ya furta wani abu yana motsawa qasan zuciyarsa.......wani abun daya motsa bacin ran dake qasan ransa ya kuma tuna masa da yadda yayita daqile yunqurin isa ga mooti din ba tare da ya bari ya sani ba,don samar masa da cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankalin da zaiyi sarautarsa ya sauke haqqi da nauyin al'ummarsa. "Mooti shine abun harinsu.......a shekaru gomar nan ba wani abu daya sauya........ta yaya zanyi bacci yadda nakeso?.....ta yaya zanyi rayuwa yadda nakeso bayan ni daya nasan da wannan yunqurin?......ka taba tunanin me yasa nake rasa sukuni duk qarshen sati idan banzo jimma ba?" Ya qarasa maganar yana zube idanunsa masu nauyi akan omari. A hankali omari ya girgiza kansa mamaki yana sake narkar dashi,da gaske kenan hasashen da yasha yi gaskiya ne.......har yanzu bai gama sanin haisam ba da gasken haka take. "Har abada......baka taba bawa maqiyi dama koda ta takin qafa guda daya tak ne!......wannan matsoracin macijin dake fakewa daga raminsa ya sadado yayi muku b'arna ya koma.......ko ya sadado da zummar cutarwa........ba murna zakuyi saboda hargaginku yana sanyashi razana ya koma ba......a'ah.....tunkararsa zakuyi......ku bishi ku zaquloshi kuma kuma illata qarfinsa......ku maida jarumtarsa zuwa tsoro da kuma rauni". Ya qarasa maganar yana jin yaqininsa da qarfin gwiwarsa akan tafiyar tana ninkuwa. A hankali omari ya dora hannunsa saman bayan hannun haisam,muryarsa a tsinke kuma can qasa yace. "Na fahimta......na fahimceka haisam......wannan aikin bana qasar Ethiopia kawai bane.....aikin yiwa kaine.....aikin bawa mooti daya zama uba a garemu gaba dayanmu kariya.......na fahimta". Musayar kallo suka yiwa juna shida omari na wasu sakanni,kafin haisam din ya saki qaramin murmushi yana gyada kai,sannan ya juya yana ci gaba da tafiya. "Sassauqar hanyar shiga kawai ta rage mana mu nema" "Zamu samu!" Omari ya fada da qarfin gwiwa hadi da saki murmushi ya biyo bayan haisam din. ★Su biyu ne rak zaune cikin farfajiyar da aka qawata da nau'in shuke shuke dake sake bawa gurin wata nutsuwa da kuma wani yanayi na musamman. Tsaf gurin yake da wata irin tsafta da ba abinda ya cakuda da shukokin gurin balle ya jirkita nau'insu kyansu da kuma tsarin su. Daga gurin daya zamana na musamman saboda xamanta kuwa.......shimfidu ne na alfarma na wasu lausasan carpet,bayan wasu manya da madaidaitan fililluka da aka yiwa ado da gashin dawisu,aka kuma rubucesu da sunan masarautar AGADEZ din. (08187255862 lu'u lu'u novel) Qaramin sharhin littafin iziyya ne a hannunta da take duba sharhin cikin wasu fasalai........ A zahiri karatun takeyi sosai,saidai kuma a bad'ini hankulanta ya kasu gurare da yawa. Hankalinta na farko yana kan yaran dake sabgarsu daga gefanta. Tun sanda suka iso momma safiyya ta fahimci sakewa da walwala sosai daga yaran. Bata samu haihuwa me yawa ba.....kaman yadda sultane bai dasu da yawa.......amma Allah ya mallaka mata jikokin da suka share mata hawayen samun yara,ba ita kadai bama......harda sultane din.....duk kuwa da cewa dukkaninsu ba wanda ya haura shekara goma sha biyu. Abu na biyu kuma hankalinta da tunaninta yana kan maganar da sukayi jiya da dare ita da falaak. "Kin kira yayarki kuwa?" A nutse falaak din ta gyada kai "Na kirata momma.......har sau biyu,amma bata daga ba bata kuma kirani ba" . Shuru momma tayi tana qoqarin boye bacin ranta. So take ta hadiye emotion dinta,don babu buqatar falaak ta fahimci komai,batason qara ciwo akan ciwo Tsakaninsu. Zuwa yanzun batasan falaak din ta sameta ko bata sameta ba?. Daidai sanda take rufe littafin gami da fidda ajiyar zuciya falaak din ke takowa gurin. Doguwar matashiya wadda duka shekarunta ba zasu haura goma sha biyar ba. Sanye take da baqar yalwatacciyar abaya data lullube ilahirin jikinta gaba daya,banda saman qafafunta da hannayenta ba abinda kake iya gani. Wasu irin kamanni ne suke bayyana kansu......wasu irin kamanni dake nuna tsakanin qarfin jini nasaba da dangantaka tsakaninta da AKHNAN. Ba kamanni na fuska ba......kamannin da bahaushe yake cewa KAMANNIN JINI,wanda girman dangantaka da nasabar jini ke nuna kanta. Kamar jini ce kawai,amma kamanni na halitta tako ina sunsha bambam,kamar yadda suka yiwa juna nisa ta fannin halaye da kuma dabi'u. Launin fatar falaak wankan tarwada ce.....amma irin me hasken nan da kadan ya rage a sanyata cikin sahun fararen mata. Tana da tsahon data dara akhnan,don idan ka kalli falaak zaka iya zaton ta haura shekarunta. Tana da sauqin kai,tana kuma da sauqin mu'amala......dukkan halaye da dabi'unta sun hau da mizanin da momma taso akhnan ce saman wannan dabi'un. Gurare kadan kadan sukayi tarayya a halayensu. Falaak nada yawan shuru shuru kaman yadda akhnan miskilanci ya zame mata cikin jini da zuciyarta. Saidai falaak nada sakewa da mutum idan ta aminta dashi ko kuma ta saba dashi har kuyi hira. Falaak nada kyauta.....girmamawa da mutunta dan adam......yayin da ba lallai ka fahimci wadannan daga gurin akhnan nan ba......don bata jibanci kowa ba......batayi mu'amala da kowa ba ballantana ka fahimci inda tasa gaba. Komai na AKHNAN din ta tsarawa kanta iya ita daya,sai wanda taso sai wanda ta gayyato sai kuma wanda ta yiwa ALFARMAR YAYI TARAYYA DA ITA. Aeeda ce ta watsar da kayan wasan hannunta,ta rugo da gudu tana nufar falaak din. Tsoro yadan shigi falaak ganin gudun da Aeeda takeyi,ta tabbatar kuma daneta zatayi idan tazo,batajin kuma tana da sauran qarfin da zata riqesu ba tare da sun fadi ba,don haka kafin Aeeda ta qaraso falaak ta durqushe a wajen tana cusa kanta tsakanin qafafunta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 29 __________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ____________________________ Cikin dariya Armelle da qarasowarta gurin kenan ta daga Aeeda cak tana dariyar da momma dake zaune daga nesa tana kallonsu itama ita takeyi. Aeeda qarfi falaak tsoro,cikin sati guda kacal da zuwan yaran sun bata wani farinciki......sun bata wani nishadi da nutsuwa,taji a jikinta tamkar tana hadewa da kammale ahalinta guri guda da wani irin kyakkyawan fata da kuma saka ran su zama wasu ababen alfaharin qasar niger da masarautar agadez din gaba daya. Falaak dake durqushe batasan me ya hana Aeeda qarasowa ba,tadaiji muryar armelle tana cewa. "Matsoraciyar uwa......ki miqe hakanan,aeeda ta barki da tsoronki". Kanta ta daga idanunta suka sauka kan armelle dake dauke da aeeda,saita saki wani gauron numfashi ta miqe tana gyara yafen mayafin abayarta da sulbin gashinta ya sakashi sulalewa ya fadi. "Kwanan nan zan fara raba hanya dake aeeda.....ke bakisan kalar qarfin da kike dashi bane?". Sosai aeeda ta riqe wuyan armelle tana dariya abinta. A shekarunta guda hudu rak da take dasu,itakam ba komai bane ma take fahimta ba,ko yanzun ma hargagin falaak dariya ya bata,ta riqe armelle da kyau wadda take nufar momma don isar mata da saqon da take dauke dashi. "Sauketa armelle......wannan inajin anya ba noma zamu koya mata ba?" Momma ta fada muryarta a washe. Dariya armelle ta saki,ta tsugunna tana sauke aeeda,wadda kaman jira takeyi ta fella ta koma wasanta abinta. Gefen momma falaak ta zauna tana mitar qarfin aeeda,momma ta kalleta kadan "Kin sake kiran yayarki?" Dakatawa da maganar falaak tayi sannan ta girgiza kanta a nutse. "Na manta momma ban sake kira ba". Dauke dubanta tayi ta mayar kan armelle. "Dauko wayata ki kiramin biftu" "In sha Allah" Armelle ta fada tana matsawa daga gefe kadan ta dawo da wayar. Shuru ne ya ratsa wajen sanda wayar ke bugawa tana ringing tare da tafiya kai tsaye zuwa wayar wanda aka kira din. *AKHNAN* Duk da cewa ranar tana cikin ranakun fitarta aiki.......amma saita soke fitarta aiki a ranar. Ta tabbatar kusan d'ai d'aikun mutane ne cikin ma'aikatan company dinta,manyan da qananan wadanda basu kalli wasan ba,ta kuma tabbatar da yawansu jiran isowarta company sukeyi. Duk da basu da wata fuska ko kuma damar da zasu iya fuskantarta da magana makamanciyar wannan......don kuwa baqon abune ganin fuskarta koda kuwa kai din dan halalin kamfanin ne. Samun damar ganinta yana ga d'ai d'aikun mutane,su dinma sai abinda ya zama dole,so ba wanda yake da cikakken access da office dinta ballantana ya samu ganinta kai tsaye. Ko ya zama dole ka ganta,to sai ka shallake wadansu mutane kafin ka samu izini da daman hakan,cikinsu harda aisa da shehnaz. Haka kawai take jinta cikin nishadi,musamman da gidan ya zamana ba 'yan takurarta aisa da shehnaz,don dukansu sun fita office ita daya ta rage. Ko da buhaina ta hada mata breakfast ma kadan taci ta koma ta kwanta abinta. Bacci tayi sosai,don da qyar ta tashi tayi sallar azahar,sannan ta zauna tana duba ayyukan dake office ta cikin system dinta. Awa biyu ta shafe kafin ta janyo waya tayi kiran barra'u. "Hadamin ruwan wanka" Ta fadi ba tare data kalleta ba tana qoqarin concluding wani report data gama summary dinsa. Cikin girmamawa ta wuce,ta kuma shirya mata toilet din,hatta da towel ta ajjiyeshi a inda ya dace,ta kuma saisaita yanayin dakin yadda zai dace da jikinta yadda takeso,sannan ta fito tana shaida mata ta kammala. Batace komai da ita ba,itama bata wani damu da hakan ba ta taka ta fice don ta turo birra ta qarasa aikinta. Da sallama birran ta shigo,ko kafin tace wani abu akhnan ta daga mata yatsunta,abinda ya alamta mata bataso tace komai.....ta wuce kawai tayi aikinta,sai ta wuce zuwa cikin. Sashen kayan sawarta ta isa,ta kuma zabi sutura kala biyar kamar kullum,ta duba bangaren undies ta ciro mata,sannan ta fito dasu ta jera mata su saman gadon. Kusan a kowacce rana hakan ce take kasancewa,birra buhaina bushira da barra'u sune duk wani motsi nata,sune komai nata. Ida akwai wani abu da akhnan ta sani shine ta zare tufafin dake jikinta ta watsar ta shiga ta wanke fatarta ta dauro jikinta da towel,sai sanya under wears dinta kawai. Wani lokacin hatta da kayan nata sai sun taimaka mata wajen sanyawa,musamman idan suka kasance ba simple dressing zatayi a ranar ba. Kamar ta fannin abinci,abinda kawai ta sani shine........ta duba me aka dafa,idan yayi mata tace su zuba mata ta tsakura ta tashi tabar gurin,idan baiyi mata ba ta saka order na wani abun a kawo mata,musamman idan 'yan sarautar suna kusa,bata sha'awar fita. Wani lokaci ma ciye ciyenta zatayi kadan taci gaba da harkarta,kasancewar sam abincin bai dameta ba. Koda taci abincin dan abinda takeci din bai kai ya kawo ba,amma hakan bai hanata jikinta da fatarta wani irin kyau murjewa da kuma daukan hankali ba,kasancewar tana ta'ammali da madara shanu data raqumi tatacciya. Ko a yanzu ma data gama system din nata kawai ta iya dauka saboda muhimmancinta tana wucewa ciki da ita. Bayan ta wuce toilet birra ta dawo ta kwashe komai ta killace,ta kuma dauke inner wears dinta ta wuce dasu zuwa laundry room don tsaftacesu kaman yadda suka saba. Da dogon towel nannade saman kanta ta fito,wanda da alama wankeshi tayi saboda yadda qananun gaban goshinta suka kwanta sosai a goshinta. Da idanu takebin kayan daya bayan daya tana son gane wanne ne ya dace da yanayinta. Qaramin tsaki taja tana ware towel din gami da zareshi daga kanta ta wurgar dashi a gefe,wannan ya bawa dogon gashinta da tsahonsa yakai har saman mazaunanta kadan bai qarasa kansu ba damar warewa. Hannu tasa ta sake daga kayan,batasan sai yaushe birra zata daina debo mata kayan da basu dace da yanayin ba. Watsar dasu tayi ta koma bakin gado ta zauna,ta jawo wayarta tana qoqarin kiran birra kan tazo ta maida kayan ta debo mata wasu kiran momma din ya shigo. Idanu ta zubawa screen din wayarta daketa motsa numbers din dake kai kawo saman screen din. Ko sau daya bata taba sha'awa ko marmarin saving number wayar matar ba. Har yanzu ta kasa jin akwai alaqa a tsakaninsu kamar yadda sultane da mammin suke fada. Zuciyarta empty take akan matar.......ko kwatar kwatar kwatar kwatar abinda takeji akan mammina babu shi ko digo a zuciyarta a kanta. Sau da dama ma tana mancewa da ita cikin rayuwarta,tana mancewa da komai daya shafeta,ciki kuwa harda falaak din. Duk da cewa yarinyar bata cikakken sati bata tabata ba,kota watsapp din da take jimawa batabi ta kansa ba,ko ta email da sauran hanyoyin tura saqonni,saboda abune me wahalan gaske ta kirata,kamar yadda itama ba zata iya tuna lokaci na qarshe data kirata din ba. (08187255862 Lu'u lu'u novel paying) Ganin kiran ya sake shigowa a karo na biyu ya sakata sakin qaramin tsaki,tana jin kamar ta dameta ne,tana da tabbacin kafin su kammala wayar saita gaya mata wani abu da zai sanya ranta ya baci. Batasan me yasa ba kullum wani irin kallo take mata,tana ganin kallon da take mata ma kaman bata aminta da zamanta a Niamey bane,tasha fadi kuma yasha shiga kunnuwanta,don matar macace da bata shakka ko shayin fadin maganar data dace da ra'ayinta,koda akan waye kuma koda a gaban waye. Muryar falaak da taji tana sallama ta sassauta mata abinda takeji a ranta. Ta amsa sallamar cikin qasaitarnan tata. "Bonsoir sœur chérié(barka da yamma lovely sister)" Falaak ta fada da wannan sanyin nata. "Chérié?(abar so?)" Akhnan ta fadi qasa qasa tana juya kalmar. So take ta fadi wani abu da zai hambarar da kalmar ko yaya ne,amma sai bakinta ya gaza furta komai. Tadan nisa kadan muryarta a nutse ta amsa mata. "Bonsoir" "Kina lafiya yaaya?.......inata kiranki ban sameki ba" Falaak ta sake fadi can qasan ranta tana jin wani abu yana motsawa game da akhnan. Duk duniya zata iya cewa ita daya ce......tana jin wannan kadaicin har cikin jininta.......duk duniya akhnan kawai zata kalla a mazaunin shaqiqiyar 'yar uwa,wadda ba wani dama komai qanqatarta da zata iya yanke ko rarrabe jinin da yake gudana jikin akhnan da irin jinin da take gudana a nata jikin. Hairaan ce ta biyu....hairaan din ce kuma tayi qoqari matuqa wajen cike mata dukkan wani gibi da takejin tana dashi,saidai akwai wannan gurbin,har yanzu akwai wannan space din da babu abinda ya cikeshi. "Je suis accupé(nayi busy)" Ta fadi a taqaice tana duban birra data shigo dakin a sannan ta kuma duqe tana jiran umarninta,sai tayi mata nuni da hannu akan ta kwashe kayan ta maidasu inda ta debo,daidai sanda falaak ke gaya mata. "Na kira mu gaisa......na gaya miki mun dawo agadez.....ni da aeeda da Aafreen". Shuru tayi tana son tuna yaran su waye?. Tasan hairaan.....tasan kuma itace mamarsu......amma sukam yaran ko cikakken kamanninsu ba zata iya tunawa ba,hasalima sunayen nasu banda yanzun falaak data fadi babu guda daya data riqe. Ta taso a matsayin 'YA GUDA.....ta taso a sansanin da babu wani yaro da ake gani......ba wani yaro da ake bawa kula gata da tarairaya.......ba wani yaro daya isa ya gilma ya gaban shugabancinta,ta gaban qaunarta.....ta gaban iko da sangartarta,da haka zuciyarta ta ginu ta wani sha'awar yaro burgewa ko qauna. Ita daya take kalla a matsayin yarinya a wancan lokacin,a yanzun kuma ita daya take kalla a mazaunin wadda ta samu dukkan soyayya. "Yayi" Ta sake amsawa a taqaice,qasan ranta tana jin meye hadinta da dukka wannan labarin?,meye alfanun da zata samu da falaak ke bata lokacinta haka?. "Yaushe zaki shigo agadez?......II y a longtemps que nous ne nous sommes pas rencountrés(mun dade bamu hadu ba)" "Pas pour le moment(ba yanzu ba).....Appelle-moi plus tard,merci(kya sake kirana wani lokacin.....na gode)" Sai ta yanke kiran tana jan siririn tsaki gami da kangarar da wayar a gefe tana matse yatsunta guri daya. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 30 __________________________ https://wa.link/l1gcz8 ASSALAMU ALAIKUM Mutanen Zuzeam ventures Ga wani sabon promo na bullo muku dashi don farin cikinku dajin dadinku Kunsan promo na na dabanne namu ba irin nasu bane hajiya ta mai kike jira da 7500 dinki ki kwashi kayan 19k 1. Rabin kazar mallaka 4500 2. ⁠married femfresh wash 2k 3. ⁠garuka 7in1 masu wata 7 ajiki 2k 4. ⁠Gumbarmadaradanonon rakumi 1500 5. ⁠Tsimin mallaka 2500 6. ⁠maganin infection 1500 7. ⁠matsin mallaka ba aba mai kishiya 5k Duka kayan 19k za a baki akan 7500 Kuma mutun 20 na farko sunada kyautar kayan 4k Matsin maida tsohuwa yarinya 1k Gumbar emergency 1k Turaren mallaka 2k Allah yaba mai rabo sa a Zuzeam ventures takuce 🥰👍🏼 Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi https://wa.link/l1gcz8 gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye ta WhatsApp 08144015291 muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 😁😁😁 https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki __________________________ Ta bangaren falaak shuru tayi,tana gaza sauke wayar daga kunnenta. Daga yadda momma safiyya taga falaak tayi tasan akwai wani abu,sai ta miqa hannu tana zare wayar a hankali daga kunnen falaak. Sosai ran falaak ya tabu,ta waiwayo a hankali tana kallon momma. Tayi zaton zataga bacin rai akan fuskar momma din......ta tsammaci zataga fushi ko nuna rashin jin dadi.....aah,a maimakon hakan murmushi taga tana yi. "Kinji haushi ko?". Ta fada tana tsare falaak da ido. Qasa falaak tayi da kanta,don batason ta yiwa momma qarya,batasom ta cewa momma bataji haushi ba. A nutse armelle ta motsa,tanason basu guri ne don ta fahimci magana ce data shafesu zasuyi,batason jin kowanne sirri nasu,duk da tana dauke da manyan sirrikan momma safiyya,to amma ita din me kamewa ce gami da fidda kanta daga dukkan sha'anin da ba'a nemi ta tsoma kanta ba. "Ki gafarceni......na katseki,malamin nan ne ya iso......an saukeshi kuma a masaukin baqi na farko,nace bari na sanar miki". Waiwayawa momma tayi tana maida hankalinta ga armelle. "Ma sha Allah......a saukeshi da dukkan nau'in abinci da nasha......a bashi uzuri ya saurareni na minti biyar zuwa goma kacal,ina fitowa". " An gama Allah shi taya miki" Armelle ta fadi tana miqewa. D'aneta aeeda tayi kuwa kam tace sai ta bita. Da murmushi a fuskar armelle ta tsugunna aeeda ta d'ane bayanta suka fice tare. "Kinji ba dadi falaak?" Momma ta sake jefawa falaak tambayar. A wannan karon falaak din dago kanta tayi kai tsaye tana duban morsa safiyya. "Don Allah momma......don Allah....." "Karki roqeni akan kada nace ki sake kiranta falaak......saidai ki canza wata buqatar.......a wadda zaki canza ma din kada ki sako batun nesanta da ita,.....kada kuma ki sako batun yanke mu'amala da ita". Momma ta fada fuskarta na komawa yanayi na gaske. Shuru falaak tayi tana duban momma din,kafin ta zare idanunta ta maida gefe tana qoqarin hadiye sosuwar da ranta yakeyi,tanason cinye zafin da taji wai ko hakan zai bata damar fuskantar abinda momma ke sln gaya mata. Duk da tasani har yau,ko sau daya bata taba fuskantar momma a irin wannan yanayi da zance irin haka zai wanzu tsakaninsu ba.......bata sani ba,momma dince bata fahimceta ba,ko kuma itace bata da fadin qirjin fahimtar momma din?. Tattausan hannun momma daya kamo nata hannun shi ya janyo hankalin falaak gareta. Idanunta suka sauka cikin na momma,take wani abu ya taso ya daki zuciyarta ya kuma karyata. Wannan raunin da ta saba gani a idanun momma......wannan raunin da bata taba ganinsa akan komai ba sai akan akhanan......akhnan din dai?,wanne irin qauna ce haka take mata?,wacce irin soyayya ce wannan?. "Falaak......ki taimakamin wajen raya wannan zumuncin.........koda bayan raina falaak ban amince ki yarda akhnan ba,koda bana raye ban yarda ki zubda zumuncinku da akhnan ba,dukkaninku abu guda ne....jini daya ne yake zagayawa a jikinku......iyayenku daya maza da mata.....kaman yadda iyayen iyayenku ma daya ne......ki taimaki wannan igiyar karta tsinke da mafi munin tsinkewa" Da sauri falaak ta kama hannuwan momma gaba daya ta riqe da kyau. Idan har da gaske tayi gani me kyau hawaye ne suke neman taruwa qasan idanun momma din nata......me yayi zafi har haka?. "Kar kice zaki zubda mana qwalla.......zata zame mana masifa momma........nayi alqawari daga yau......kome yaaya zatayi......kome zata yimin ba zaki sake ganin koda bacin raina ba......zanyi saboda ke......zanyi saboda sultane......zanyi saboda zumuncin". Wani murmushi dake cakude da wani irin pain morsa safiyya ta saki,ta jawo falaak jikin ta ta rungumeta tana fadin. "Allah yayi muku albarka,ya shiryamin ku......ya baku nagartattun mazajen da zasu riqe mana ku bisa amana,su kama hannuwanku su doraku akan tafarki madaidaici". Har can tsakiyar zuciyarta addu'ar momman ke ratsawa,tana jin wani qarin nutsuwa da kuma relief sosai a zuciyarta. ★Cikin tarin nutsuwar nan tata take takowa gaban nanay din. Hannunta dauke da madaidaicin kwanon da yafi kama da akushin da aka zamanantar dashi da ado da kuma tambarin dake nuna sarautar JIMMA. Kanta a qasa ta qaraso gabanta,ta tsugunna a hankali ta ajiye kwanon gabanta. "galatoomaa(na gode)" Nanay ta fada cikin murmushi tana duban samee data zame a hankali kanta a qasa ta zauna a gabanta. Bude kwanon tayi wanda ke dauke da dafaffen maganinta da wasu irin ganyayyaki dake qarawa masu shekaru irin nata kuzari da kyan jiki. Yankin jimma manoma ne na gaske.....manoman da bawai iya abinci kadai suke komawa ba.....aah,hatta da coffee tarin magungunan da qasashen turawake rububin zuwa siyan ganyayyakin su kuma maidasu maganin bature......irin wannan abun ya sanyawa haisam tunanin bude makeken kamfanin sarrafa magunguna......wannan tunanin ya sanyashi saka Aadel da hussam karantar pharmacy. Bismillah tayi,ta dauki maganin tasha sau uku sannan ta ajiye,samee ta matso ta dauki murfin ta rufe sannan ta maidashi gefe,har a sannan idanun nanay suna kanta. "Samee" Nanay ta kirata,har cikin jikinta taji kiran,tayi kaman zata dubeta amma ta kasa,saita amsa kiran tana maida kanta qasa. Maganganu ne sosai a ran nanay da takeso tayi da samee.....amma kafin tace wani abu kira ya shigo wayarta dake aje a gefe,kiran daya dauki hankulansu su duka ita da samee din. Tana karance da ita,daga yadda taga reaction na samee din ya gaya mata me kiran tun kafin takai ga qarasa miqo mata wayar,ta miqa matan da wani irin sanyin jiki sannan ta soma takawa zata fice don basu guri. "Koma ki zauna" Nanay ta fada a nutse tana daga kiran sannan ta kara a kunnenta. "Wa'alaikumussalam warahmatullah" Ya maidawa nanay martanin sallamartata da muryar nan tasa dake cike da wani irin sauti me fusgar hankali da kunnuwa,walau karatun qur'ani yakeyi ko magana yakeyi dakai. "Akkam jirta nanay?(kina lafiya nanay?)" "am fine hojjechaa jira alhamdulillah(ina lafiya alhamdulillah)". Sassanyar ajiyar zuciya ya sauke yana sauke qafafunsa daga saman lallausan gadon nasa. A duk sanda zai matsa daga inda suke koda na kwana d'aya ne......sai ya dinga jin kamar wani abu zai samesu. Ya sani wannan din tasirin shaidanne......don yayi imani yayi kuma yaqinin ba abinda ya isa ya samu wani bawa saida nufin ubangiji. "Komai lafiya lau nanay?" Ya sake tambayarta yana dubansa kansa cikin madubin daya koma gabansa ya zauna. Armless shirt ce a jikinsa sakakkiya,sai wandon daya sanya da duka duka iyakacinsa qaurinsa,ya zarta gwiwa amma baikai idon sahu ba. Dukkan kayan baqaqe ne sidik,cotton masu dauke da tambarin kamfanin LV wato. "Muna cikin amincin Allah Muhammad". " Ma sha Allah" Ya amsa mata yana aza hannunsa saman gashin dake habarsa da kuma kuncinsa. Yana wassafa ta yadda zaiyi magana ne da nanay......ta yadda zata kuma fahimceshi da kyau. "Magana kakeso kayi muhammadu......gayamin me yake faruwa". Lumsassun idanunshi ya lumshe,wani qwataccen murmushi yana subuce masa. Nanay ta daban ce......wata irin uwa da tasha banban da dukka uwayen daya sani,nanay kyauta ce daga Allah,tana iya fahimtar maganar da d'anta yake mata da kowanne yare. Idan yace yare bawai yana magana akan yare na harshe ba,yare na yanayi.....yare na gabbai da kuma yare na motsi. Qafafunsa ya aza saman stool din dake gabansa,yayi relaxing sosai cikin kujerar sannan ya fara mata bayani. Batace komai dashi ba harya kammala. Shurun nata har yayi yawan da sai daya kira sunanta. "Nanay?" "Tunani nake muhammadu". " Karkiyi tunanin komai Nanay.....Allah shine me rayuwa.....shi yake tsarewa". "Muna fata kuma yaci gaba da tsarewar.......wacce qasa ce muhammadu?" Ta tambayeshi a karye. "Niger agadez". Wani siririyar faduwar gaba ta saukar mata. Kiran sunan qasar hade da garin ya zame mata tamkar wani tuni akayi mata.....tuni a KANTA.....fuskar da har yanzu taqi bacewa cikin idanunta.....kaman yadda sautin muryarta taqi bacewa daga kunnuwanta. "Agadez muhammadu?" "Eh nanay......da wani abu ne?" Kai ta girgiza a hankali,saita zarce da jan hankalinsa kamar yadda ta saba,da rufewa da tarin addu'o'i. "Kada kace zaka rufemin komai bayan tafiyarka......ina da buqatar sanin kowanne hali kake ciki......inaso a wannan karan na zama qawarka kuma abokiyar shawararka fiye da ko yaushe.....Allah ya albarkaci rayuwarku gaba daya". " Ameen nanay " Ya amsa yana lumshe idanunsa. Haka kawai yaji zuciyarsa kamar tayi rauni kadan,ya sani a yanzun idan aka zubewa nanay zabin ya tafi ko ya zauna.....tabbas da gudu zata zabi ya zauna din,saidai wannan tafiyar nada tarin muhimmanci a rayuwarsu gaba daya.....amma yana sanya ran tafiyar ta zama ta qarshe da zata kasa samar da gamsuwa cikin zuciyar nanay kamar yanzun. Yana shirin ajiye wayar tasa ya fahimci da shigowar sabon saqon email. Budeta yayi ya kuma wuce kai tsaye zuwa gmail dinsa. Da sauri ya aje qafafunsa qasa yana bude lumsassun idanunshi da dukka girmansu. "Welcome to NIAMEY horse race........you're successful registered to the special horse race batch 2 and final.....muhammad ja'afar". Sau uku yana maimaita karanta email din da baisan daga inda ya fado ba......saidai a iliminsa na karatun na'ura me qwaqwalwa,bata yadda za'ayi saqon haka kawai ya fado email address dinsa saida wani dalili. Omari na ya fado a ransa,sai ya sauka da dukkan nutsuwarsa ya sanya lallausan bedroom slippers dinsa ya fara takawa a hankali ya nufi balcony din da ya baro Omari din dazu a zaune yana qoqarin tattara bayanai. Sama sama yake jiyo muryar omarin,da alama waya yakeyi,kuma wayar ta masa dadi da gaske,don kuwa yana iya jin fitar sautin dariyarsa. Yana dab da shiga balcony din ya fahimci conference call yakeyi shi dasu mutallab naseeb khadeem da Amjad,muryar maleek ne kawai bai samu jiyowa ba. (08187255862 lu'u lu'u novel paying) "Yauwa......gashinan ma" Omari ya fada yana karkato da fuskar system din saitinsa sanda yake qoqarin zama saman bean bag din dake gefan omari. Zama yayi Normal zama a wajensa......amma a idanun me kallonshi zama ne dake nuna zallar qasaita da sarauta dake yawo a jininsa. Murmushi Amjad ya saki daga allon system din yana duban haisam. "Ya zame maka jiki.....yabi jikinka da kyau......yanzun idan nace wani qasaitaccen zama kayi fa ba zaka yarda ba" Dukkaninsu dariya suka sanya,abinda ya sanya haisam fidda wani siririn miskilin murmushi yana kuma gyara zaman nasa daga yadda yake a dazun. "A'aha......an kuma dai" Mutallab ya fada yana duban haisam din. A wannan karon dole suka sanya ainihin murmushi subuce masa,wanda har sai da jerarrun fararen haqoransa suka bayyana. "Ba zaku canza hali bane?" Haisam din ya fadi da wani irin nutsuwa wadda tun asali tasa ta bambanta da tasu. "Indai akan fadin gaskiya ne ba zamu canza ba......ina aka kwana ne?......ba wani labari?" Mutallab ya tambaya yana karbar cup daga hannun matarsa wanda iya hannunsa ne kawai daya miqa ya karba cup din ya bayyana. Hannu haisam ya aza saman sumarshi yana shafata a nutse,yasan me haisam ke nufi,indai yace ba wani labari?.....to da gaske yake,yana son yaji labarin yayi budurwa......ko ya samu matar aure. "Akwai labarai" Omari ya fada da sauri sannan ya dawo da fuskar system din saitinsa. Idanu haisam ya zube ma omari,wanda sosai yaji a jikinsa haisam din ya kafeshi ne da wadannan mayatattun idanuwan nasa,shi kuma a yanzun bayajin akwai abinda zai dakatar dashi daga bawa su Amjad wannan labarin,musamman da signal ya harba ya nuna amsa maleek ma ya iso online. Hannu kawai haisam ya miqe ya bame fuskar system din ya hadeta da juna yana tsare omari da ido bayan ya danne mic din. "Me kakeson gaya musu?,labarin qanzon kurege?" Yayi maganar yana dage masa dukka girarsa biyun ba yare daya dauke hannunsa daga system din ba. Shima girar ya dage masa masa dariya tana kubce masa. "Idan kai baka sonsu su suna sonka ai......ya kamata a nema musu tallafin masu yi musu campaign ko zaa dace daya a cikin su suyi wuf dakai.....ko duka biyun ma" "Biyu.....waye da waye." "Saami da Menelik". Sosai ya tsaya yana duban omari. "Wato har qwaqwafinka yakai can omari?" Dariya sosai omari din ya saki ganin yadda haisam din ya hade rai da gasken gaske. Dariyar omarin ta fara isarsa,ya kuma tabbatar a yanzu haka sunbar su maleek akan layi,sai ya saki siririn tsaki ya dauki system din yana riqeta a hannunsa,sannan ya bude screen din yan zarcewa zuwa wani parlor din daban. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 31 *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX Saman ottoman ya zauna,ya jawo wani ya dora system din akai yana goye hannuwansa a qirjinsa sanda fuskokinsu dukkaninsu suka fito tarwai cikin screen din. Har hada baki sukeyi wajen tambayarsa wanne labarin omari zai basu?. Hannuwansa ya watsa yana cin serious. "Bani nace xan baku labari ba......saiku jira parrot din yazo ya baku" Dariya suka saki kafin maleek yace. "Ranar Saturday din zaka sauka agadez din?.....qarfe nawa race din zai fara?.......ya zama dole muje mu nuna solidarity". Idanu waje haisam ke kallonsu ganin yadda suka barke da maganar da zancan tseren dawakan. "Hi guys" Ya fada da Sassanyar muryarnan tasa da yakanyi amfani da ita wani lokaci yana daga fararen hannuwansa. Dukka hankalinsu suka bashi. "Wanne race kuma?" Ya kuma tambaya yana baza idanunshi a tsakaninsu. "Look man......wannan wani abune na daban a qasar daba tamu ba.......ba kuma haramun bane bare ka haramta mana zuwa......so please bama buqatar wani sharhinka okay?" Khadeem ya fada yana dage dukka girarsa,kafin kuma ya sake cewa wani abu khadeem yayi off,sai dukka yaga kowannensu yayi off,alamun zuwa kenan ba gudu ba ja da baya. Shuru yayi ya zubawa system din da kowa yayi off ido yana dubanta. Yana jin kamar hadin bai dace ba,bai kamata Omari yayi wannan hadin a qasar da suke da gagarumin aiki a cikinta ba,sai yayi shutting down na system din ya dauketa cak ya nufi dakin da omari yake sauka. A nutse ya tura ya shiga,sai ya sameshi saman abun sallah yana raka'ar qarshe,da alama wuturi yakeyi(sallar wuturi nada matuqar muhimmanci sosai.......Allah yana sonta,koda baki da daman sallar dare,kiyi wuturi kafin ki kwanta). Koda ya sallame sai ya juyo yana duban haisam din. "Wanne irin ganganci ne wannan omari?,wanne irin kuskure ne haka?". Zama yayi sosai saman abun sallar bayan ya juyo yana duban haisam din. "Hanya muke nema a sauqaqe ta shiga garin agadez cikin yanayin da zai badda hankulan mutane......ba wata hanya mafi sauqi sai wannan.....sassauqar hanyar da zata bamu daman sajewa da 'yan garin a cikin sauqi". Shuru haisam yayi yana juya maganar taren da jefata nisan nisan hankali da kuma mizanin da zaiyi daidai da ita. Shurun da haisam yayi bai sanya omari katse shurun ko katse masa tunani ba. Don ya tabbatar a dukka shurun haisam din akwai dogon nazari da hangen nesa . "Wannan action din naka zai iya calling attention na wadanda bai kamata ba......ka gane mana omari" Duban haisam ya sakeyi kafin yayi qasa da kansa yana dafe hannunsa guda daya da kan nasa. Sai a yanzu da haisam yayi maganar da wannan yanayin ya tuna da abinda ya kamata ace ya tuna dashi din kafin wannan lokacin. Tun suna da qananun shekaru mooti ya hana haisam shiga kowacce gasar tseren doki,saboda wani irin maita da yake dashi gurin qurewa doki gudu. Ya qware sosai irin qwarewar data sanya nanay ta yiwa mooti magana akan BAKI. "Ina tsoron baki akan muhammad......baki gaskiya ne Allah ya taimakeka,a duk sanda zai shiga wata gasa shike zama na daya,kada baki ya kassara mana shi". Sosai mooti ya fahimceta,ya kuma fahimci inda ta sanya gaba,take kuma ya hana haisam shiga kowanne gasa bama ta doki kawai ba. (Wannan din wani kariya ce data kamata kowanne iyaye su bawa yaransu,bawai kayita murna yarona ta daya yake zuwa ba....yarona ya iya kaza,ai yarona yayi mugun iya kaza.......baki baki masifa ne akan 'ya'yanmu,baiwar da Allah ya yiwa yaronka boyeta kakeyi,har sai sanda ya isa munzalin da duniya zata gani,baki gaskiya ne.....wani baisan kuma yana dashi ba,koda yaronka ne ka rage tankashi,don akwai da dama iyayen da suka cinye yaransu da bakinsu suka gusar da wata baiwa ta kyau yawan gashi ko farinjinin jama'a da yake dashi,dake da ubansa kansa ku rage tanka yaranki,Allah ya bamu kariya da tsari irin nasa ameen summa ameen). "Na riga na shigar da komai.....sunyi approving kuma......yanzu mene abunyi?" Omari ya fada yana bawa haisam dukka hankalinsa. Ajiyar zuciya ya sauke yana sauke hannayensa qasa "Zan gani......zanyi dukkan qoqari wajen ganin komai ya tafi daidai ba tare da wata matsala ba" Ya fada yana miqewa hadi da zube hannayensa a aljihun wandonsa. "Me gaminka da English ne?" Omari ya tambayi haisam din yana cire hular kanshi ya aza saman abun sallar da yake kai. Juyawa haisam din yayi a nutse,kaman bazai tanka masa ba,har sai da ya kai dab da qofa "Idan baka da siffofi mabanbanta ka sani baka cika mizanin zama ma'aikacin NISS ba...........dole ka zama a duniyarka,dole kuma ka zama a wata duniya ta daban da taka". Shuru omari yayi yana bin hanyar da haisam ya fita da kallo,murmushi na fita kadan kadan daga fuskarsa. Shi din shaida ne......kyakkyawar shaida kuma me cike da tabbacin muhammad haisam ya banbanta da mutane masu tarin yawa........idan maganar intelligence akeyi nashi na dabanne......komai nasa tamkar an zabar masa ne.....kamar haka yaso ya kasance. ★★*NANAY* Boyayyar ajiyar zuciya ta sauke tana gyara zamanta idanunta suna kan saami. "Saamirah" Ta kira sunanta a tausashe,abinda ya sauke saukar da nauyi ga jiki da zuciyar sameera din kenan. "Na'aam nanay" Ta amsa ba tare data iya daga idanu ta kalleta ba. "Saamee......kada ki saka rai me yawa......kada kuma ki saka buri da yawa,amma kuma kada ki sare,kada kice kin gaza,kada kuma kice zaki daina har sai kin cimma burinki......". Wani faduwar gaba dukka maganganun nanay suka saukar mata dashi. Kunya da nauyi suka wani irin dabaibayeta,tana jin kamar ba zata iya motsawa daga inda take ba. Kada dai ace hatta da nanay ta fuskanci abinda ke zuciyarta?,dama kallonta kawai nanay keyi?. Yanayin yadda saami din ta takura cikin tsangwamar kanta ya sanya nanay sakin boyayyen murmushi. "Koda ban haifeki ba saame ina iya fuskantar wasu al'amura daga yaran da suma ba nice na haifesu ba,ke din amana ce a hannunmu saami,dole mu sanya idanu a duk wani motsi naki kaman yadda zamu sanya akan na yaranmu........haisam......yaro ne da ban taba hasashen samun kyautar Allah kamarshi ba,yana da wasu nagartattun halaye da nayi imanin ba zaki wulaqanta ba,ba kuma zai wulaqantaki ba saboda kina sonshi.......amma yana da kebantattun halaye da suka sha banbam dana sauran abokan rayuwarsa.....yana da zabi.......yana da kuma irin nashi yanayin.....ko bayan haka ma gaba daya,zanso ko wacece zata shiga rayuwar haisam ta fara samun soyayyarsa tukunna......ta nemi soyayyarsa da kanta kafin ta kutsa kai cikin rayuwarsa,wannan ne kadai zai sanya ta fahimceshi,ta bashi uzuri,ta bashi cikakkiyar kariya a kowanne irin yanayi,irin kariya da nutsuwar da kowacce mace ta gari take bawa mijinta......" Sai tayi shuru tana maida numfashi,tana ganin yadda maganar ke samun kyakkyawan matsugunni a zuciya da kuma hankalin saame din. "Zanso a sanda zaki shiga rayuwar haisam ki shiga da dukkan daraja da martabarki ta diya mace,kaman yadda zan sowa yaran da na haifesu a ciki na.....zanso ki samu wannan martabar da mutuntawar.......kin cancanta saami,kina da kowanne irin quality da namiji ke buqata a gurin mace,bana haufin watan watarana zaki samu wannan gurbin......zaki samu wannan muhallin......za kuma ki samu wannan darajar......wannan matsayin da kuma wannan matakin". Har tsakiyar zuciyarta takejin wani abu me sanyi yana kwarara mata da kalaman nanay,bata tana zaton haka abun zaizo da sauqi ba daga bangaren Nanay,duk da ita din me sauqi ce.......sai gashi yazo mata da sauqin fiye da yadda ta zata ko tayi hasashe ma. "Na gode nanay.....na gode" Ta fada cikin matsananciyar kunyar data sanya takejin ba zata iya tashi tayi tafiya a gaban nanay ba. ★banda Dim light din da dakin yake bayarwa,ba wani sauran haske ko fitila data rage idan ka cire ta system din dake gabanta. Su ukune cikin dakin,tsakanin qarfe goma zuwa goma da rabi na daren ranar. Aisa akhnan da kuma shehinaz......kusan dukkansu su ukun,duk da suna zaune ne a mabanbamtan kujeru amma hankulansu yana kan system din dake gabansu wadda ta nuna maballai biyu. ACCEPT da kuma REJECT. A yadda suke zaunen da yadda dakin ya dauki wani irin shuru saika rantse da Allah suna tsoron suyi qwaqwaran motsi kada wani abu me matuqar firgici ya dirar musu. Blue eyes dinta da hasken system din ya qarawa wani irin haske me qyalli kawai take rabawa tsakanin fuskokin aisa da shehinaz wadanda suma junansu take kallo. Tashi tayi ta zauna sosai tana sake fuskantar system din,sannan ta miqa hannu a nutse ta dannan maballin ACCEPT din,abinda ya sanya aisa fidda dukka idanunta waje tana dubanta. "Biftu......kinsan me kikayi kuwa?" Zagayayyun idanunta ta daga a nutse hankali kwance ta zubewa aisa su,ta lumshesu sannan ta budesu,wanda iya hakan ya sanarwa da aisa tana nufin eh......nasan me nayi. "Akhnan........wancan lokacin fa.......alfarma....." "Alfarma?" Akhnan ta fada a nutse tana dauke hannunta daga saman system din tana zubewa aisa su a karo na biyu. "Alfarma aisa?......" Ta sake maimaitawa tana maida bayanta jikin kujerar tayi relaxing tana fidda manyan idanunta waje. "Akwai wani abu dama da za'a yiwa akhnan alfarmarsa a duk duniyar nan?" Ta qarashe maganar da sigar mamaki cikin muryarta. Duban juna suke ita da aisa na wasu sakanni,kafin aisa din ta dauke kallonta daga kanta "Alfarma ko ba alfarma ba.....koma meye biftu,last time nayi kawaici ne kawai,kina tunanin idan sultane yaji kina shiga irin wadannan abubuwan ko mu zamu kubuta daga laifi a gurinsa?" Ta qarashe maganar tana dubanta sosai itama. Yatsunta kawai akhnan take muzawa,ko meye aisa zata fada....ko meye aisa zata ce ta fadi din......daidai da ita ne,amma ta janye kalmar alfarma a maganarta,shine kadai abinda zai sanya ta fahimceta. "Alfarma aisa....." Ta sake fada tana duban tafin hannunta da rashin hasken dakin yasa bata iya ganinsa sosai. "Yes" Aisa ta fada kanta tsaye. Shuru ya kuma wanzuwa tsakaninsu,cikin qasa da minti daya ta yunquro da wani irin zafi zafi a muryarta. "Yayi daidai.....kici gaba da alfarma din ko kada kici gaba.....ki zabi duk abinda kika zaba......koda wannan shine tsere na qarshe da zanyi sai na yishi" Akhnan ta fada tana soma sarrafa system din da zafi zafi tana cike duk wani abu daya kamata ta cike tayi submitting. (08187255862 lu'u lu'u paying) Ita kanta tasan cikin murna da alfaharin sake amsar gayyatarta suke,saboda ta tabbatar wani abu ne da bazasu taba tunanin zai yuwu ba. "Haka kika ce?" Aisa ta fada ranta a bace sosai. "Haba aisa mana......mubi komai a hankali don Allah" Shehinaz ta fada karon farko tana duban aisa din. Tsam Aisa ta miqe tana dubansu,kafin ta ajiye kallonta na qarshe akan shehinaz. "Ko meye zai faru......kada sunana ya fito a ciki gurin sultane ko nannie......babu Aisa a ciki sam". Daga haka tayi gaba abinta ba tare data ko waiwaye su ba. Shehinaz ta wannan bangaren,duk da irin sabaninsu a abubuwa da dama ita da akhnan.......amma ta wasu fannonin a ra'ayinsu da kawunansu yafi zuwa daya. Kamar a wannan bangaren......shehinaz mutum ce mesonh abubuwan da zasu bata nishadi gami da sakata walwala,don haka tseren ke nishadantar da ita itama,to amma ita kanta ba zataso sunanta ya fita wajen sultane da nannie ba.......ga morsa a gefe data tabbatar azabarta zata iya shafe ta kowa. "Akhnan" Shehinaz ta kirata da nufin gwada kwatanta mata bayanin tabar wannan race din. "Kada kice komai.......na gama cike komai na tura musu......damuwata daya shine......bansan abokin kara wasan ba......bansan wanne me gangancin bane yakeson sai munyi wannan wasan ba......na tabbatar nayi kuma imanin yayi hakanne don ya zubar dani,ya kuma ramawa wadanda na zubar haushinsu a kaina" Akhnan ta fada a nutse tana sake duba bayanai a kansa,saidai kuma blank take gani,don babu koda cikakken sunansa ma bare wani abu daya shafu tarihin wasannin daya taba yi,wanda wannan shine ita kuma zai bata nata hasken.. Abinda ya dauki hankalin shehinaz kenan itama,ta manta ma da batun bawa akhnan shawarar ta haqura din,suka shiga bincike akan komai daya shafi abokin wasan,saidai har suka gaji da ita da itan ba wanda ya samu komai a kansa. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 32 *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX _____________________________ "Na tabbatar akwai manufarsa........bawai hakanan komai ya tsara kanshi ba.......amma na yiwa kaina alqawarin saina bashi kunya kamar yadda sauran na bayanshi suka kunyata" Ta fadi tana rufe system din cikin cin matsanancin alwashi. Alwashin da ko a wancan wasan bataji tana da sha'awar ta cishi ba,tunda wancan wasan wasane kawai da ita a karan kanta ta yishi ne kawai saboda nishadi,sabanin wannan da taji yana neman canza salo. ★Cikin kwanakin ta rufe duk wani hanya ko dalili da zai sanya a nemeta a agadez........ta kuma maida hankalinta wajen gwaji da qara qwarara kanta a babban filin dake cikin gidanta. Sam bata kawo aisa a matsalarta ba,bata ma sake bi ta kanta ba. Ba wannan ne karon farko da suke samun sabani irin haka ba,kuma suzo su shirya kansu kaman bai taba faruwa ba. Duk yadda aisa takai ga cika baki tasan ba zata iya komai ba,ba zata iya tona mata asiri ba. Ba kuma aisa kadai ba,a tsakaninsu su ukunñ babu wani wanda yake iya tonawa asirin dan uwansa,kowanne irin laifi daya kuwa yayi,wannan ya sanya nannie ke kiransu da MUNAFUKAN 'YAN UWA. Sunan yana bawa sultane dariya,ya sani gaskiya anne ta fada,kuma sunan ya dace dasu,amma yakance "Ayi musu haquri,a canza musu suna". ★★★ *HIPPODROME NIAMEY*★★★ Duk girma fadi da tsahon gurin amma hakan bai hana mutane cike gurin cif cif ba. Wani irin cika gurin yayi,irin cikar da bai taba yin irinta ba a tarihin gurin. Gurin kuwa baiyi cikar banza ba,don kuwa wasan ya zama wani na musamman,fiye da ma da wasan da akayi wancan satin. Ninkin mutanen da sukazo wancan wasanne suka halasci wannan wasan,don da yawa gulma ta fita game da wacece 'yar wasan......sunanta da sunan mahaifinta,harda tambarinta a matsayinta na mamallakiyar katafaren kamfanin suturun mata masu aji.....mata masu abun hannu wato SAHEL COUTURE. Mintina talatin din farko kawai akayi aka tafi hutun farko,amma sai mintunan suka zama wasu na musamman a zukata da idanun 'yan kallo. Kamar yadda suka zama na musamman a wajen akhnan da wani madaukakin farinciki ganin score din data samu tun a zagayen farko. Wani irin wasa daya zama baqo a idanun masu kallo......su biyu ne rak mahayan......wadanda gaba dayansu ba wanda kake iya ganin fuskarsa saboda helmet din dake kawunansu. Mahayin doki na farko kana dubansa zaka fahimci namiji ne,saboda qira da zubin jikinsa daya bayyana a kayan hawan dokin dake jikinsa.....yayin da ta biyu ta fita a suffar mace sak......tun daga yanayin qirarta da kuma launin suturar jikinta. Yana sane yake bada dukkan wata dama ga abokin karawarsa.......ba tare daya tantance macace ko namiji ba......yana sane yake dage qafa saboda ba nasarar tseran dawakai bace ta shigo dashi niger........nasarar aikin hukumar binciken sirri ne ya kawoshi. Cikin muhallin da aka basu saboda hutun mintunan,hakeem ne ya miqa masa bottle na ruwa,cikin murya qasa qasa yace. "Sun saka hope da yawa akan dan wasansu......ban tantance sunan na mace bane ko na namiji.......amma da alama yana da cika baki da yawa......kayi wani abu mana akai" Hakeem ya qarasa fada qasa qasa yana ranqwafa kanshi saitin haisam. Haisam din baice komai ba illa karbar ruwan da yayi. Sam wasan ba shine a gabansa ba,ba wanda kuma zai fahimci hakan a cikin su,bayaso kuma su fahimta din,faduwa ko nasarar bashi yake hange ba,yadda a yau zasu fice daga Niamey,subi jirgin da zai sauka a agadez kai tsaye ne damuwarsa. "Hakeem" Ya kira sunansa a nutse. "I beg you" Hakeem ya fada da yaren turanci yana hadewa haisam hannuwansa guri guda. Cikin wani irin nishadi ta sauke helmet din nata tana ajiyeta a gefe. Gashinta ta kama ta tattarashi da kyau tana daureshi,fuskarta washe da wata irin fara'a da take jinta har tsokar zuciyarta. Dukka kunnenta suna sauraren bayanan Shehinaz dake kwatanta mata yadda take sarrafa thunder da wani irin qwarewa gami da miqa mata ruwa. Sai data saki miskilin murmurshin da iya sakin da fuskarta kadai tayi shine kawai zai alamta maka murmurshi tayi. Ita kanta basai an gaya mata ba.......wasan yayi mata ba zata,saboda yazo mata da wani irin sauqi da bata taba zata ba. Ta zaci abun zai zame mata me tsananin wahala walagigi dashi,sai gashi cikin sauqi tanata samun damarmakin wuceshi. Da farko sanda yake fitowa don hawa nashi dokin sanye da helmet data hana mata ganin fuskarsa ta tsorata,sosai gabanta ya fadi,wata irin baquwar faduwar gaba da bata san da ita ba. Ba yau ta saba ganin maza giant ba,Giant ne kuma ingarman da tsaiwarsa kawai zata baka labarin jarumtar dake gangar jikinsa da zuciyarsa,batasan me yasa take jin wani irin kwarjini yana hudata ba,wani irin yanayi da ya sanya tun a farko ta dinga jin faduw warwas a gasar. Faduwarta kuma daidai yake da kafawa kanta da kanta tarihin abun kunya......kamar ita zai zamana wani babban abun Allah wadai ace wani da batasan ko wayeshi ya cinyeta a wasan da wancan satin ta zamana cikin tafin hannunta. Izzarta da qasaitarta tana tare da ita,tana kuma zagayawa a jininta,wannan ya sanya taqi maida hankalinta ko idanunta ta sake kallonsa koda sau daya ne kuwa. Sai a yanzun cikin maganganun Shehinaz ta samu amsar "Ko sau daya bai kalleki ba bare har ya damu da yadda kike tsere masa.......wallahi wannan ko waye shu'umi ne......kuma bansan me yasa bai dauki hankalinsa ya dora akan race din ba" Kai ta jinjina,ranta kuma ya fara mata saqe saqe. Ko yaya ne bata son taci nasara cikin sauqi......ko yaya ne tana son su gwabza......tana sha'awar su fafata ta finciki nasararta koda tsiya ne a hannunsa. Abu na biyu ta sanya masa qatotuwar ayar tambaya......anya ba wani shiri a qasa?. Bata da wani zabi illa ta san yadda zata tona koma meye a zuciyarsa a wannan zagayen qarshen. Saidai kuma akwai wani abu daya da tayi noticing.......ta fahimci kamar akwai wani sirrintaccen sirri tattare dashi......sirrin da ya zuba masa wani irin kwarjini na musamman. Bata iya ganin komai nashi,koda kuwa hannuwansa ne dake lullube da safar hannu irin ta masu hawan dawakai......hakanan qafafunsa ballantana fuskarshi,amma tana jin wani abu me nauyi game dashi "Matso kiji Shehinaz" Akhnan ta fada tana murmushi gami da yafito Shehinaz din. ★Cikin sarewa gami da son wasan yazo qarshe hakanan ya sake hawa dokin. Saidai tun wasan baiyi nisa ba waqen da kambamar qasar da al'ummar gurin suka fara yi ya soma ruda kwanyarsa. Yana da wani irin kishin qasa da ya sanya sake zama na musamman a NISS......yana da kishin qasar da baya yarda ko ya aminta ka zagi ko kaci mutuncin qasarsa.......qasarsa nada muhimmanci a wajensa. A hankali tutocin qasar niger suka fara dagawa a gurin,suka soma yiwa gurin rumfa saboda dukka wanda yake kallon wasan ya gama yiwa wasan alqalanci. Bata yadda za'ayi abokin buga wasan ya farke wannan wasan,sun gama miqa wuyan bai iya komai a wasan ba.......akhnan din ita ke da nasara......da gaske ita din kallabi ce tsakanin rawuna. Wuceshi da tayi da waiwayowa da tayi ta masa wani sign da hannuwanta ya fusgi hankalinsa. Abubuwa guda biyu ne suka tabashi. Na farko sign din data masa alamun raini ne ga duk wanda ke buga wasan horse race........abu na biyu kuma har cikin jikinsa yaji hasashen da yakeyi tun dazun......yanayin da jikinsa yake bashi yaji yana sake tabbata. Tun dazu jikinsa yake bashi wannan din da suke wasan macace,ba namiji bace,yanayin sarrafa dokinta da yanayin sarrafawar mace yayi masa kama. "Me yasa omari?" Yaji ranshi yana baci da abinda omari yayi masa. A hankali idanunsa suka sauka akan team dinsa.....maleek,mutallab,omari,amjad,khaleed,khadeem. Tutar Ethiopia suka ware me fadi sosai.....kowannensu kuma yana riqe da wani bangare nata,sun kuma dan bada tazara a tsakanin su,abinda ya bawa tutar damar bayyana sosai. Idanunsa ya zare a hankali,qasaitaccen murmushin nan nasa yana kubce masa,take yadda ya dauki wasan a ransa ya canza cikin qasa da second biyar. Ko basu ce komai ba yasan me suke nufi.....yasan saqon da sukeson aika masa. A wajensa ba wani wasa bane me muhimmanci ba,wasa ne na samun damar shiga agadez da niger gaba daya ba tare da kowa ya gane ba.......amma a yanzun a ranshi shima yana jin koda hakanne,bai kamata ya bari qasarsa tasha kayi ba,bai kamata qasarsa taji kunya ba. A yanzun su suke wakiltar Ethiopia gaba daya,duk da duka dukansu a filin irgen yatsun hannu ne......amma ya kamata su barwa al'ummar niger suna da tambarin ETHIOPIA. Ta saki jiki sosai,ta kuma bada amanna tana sarrafa dokinta hankali kwance......saijin iskar wucewarsa tayi,kafin tayi kowanne yunquri kuma ya soma mata nisan daya sanya hankalinta tashi,ta kuma qarawa thunder qaimi. Murmushi ya sake ajewa ta cikin helmet dinsa,yana iya jiyo sautin takun dokinta,koda bai waiwaya ba kuma yana iya qididdige adadin tazarar data rage da zata iya bata damar taddoshi,don haka sai yayi mata qofar rago kawai. Tana daf da iskoshi ya sake bata badda mata tunani,ya cilla da wani irin salo daya dauki hankalin kowa,ya sanya filin yin shuru ba tare da kowa ya shirya ba,ya kuma sauya akalar magana da tunanin me sharhin dake can sama yana ganin yadda abubuwa suke so su canza a mintunan qarshe na wasan. Wani irin wasa da hankali ya soma yi da ita,wani walagigi ya fara yi da nutsuwarta da dukkan qwarewarta. Cikin mintuna qalilan gaba days ya ruda tunanin ya kuma rudata. Tsalle kawai zuciyarta keyi cikin qirjinta,wani irin tsoro taji yana saukar mata. Tunda take bata taba ganin salo irin wannan ba,ya toshe duk wani tunanin ta inda zata cimmashi ma bare ta gotashi......ya toshe duk wata kafa da zata tsammaci nasararta a kusa. Fargabarta ta sake qaruwa da ganin adadin qananun mintunan da suka rage wasan ya tashi gaba daya..... Tashin hankali ne taji yana lullubeta a hankali,RASHIN NASARA yana daya daga cikin tarin abubuwan data tsana.......ta tsani FADUWA ta kuma tsani A FITA. Ta rayu ne a saman nasara......ta rayu a tudun fifiko,ta bude idanunta ne ta tsinci rayuwarta saman ta wasu......ta tsinci rayuwarta a qulle data wasu.....ba zata taba lamunta ba ace wani can yazo ya kunyatata a tsakiyar 'yan qasarta ba......a gaban talakawansu ba........wannan ya bata qaimin data miqe saman dokin ta kuma bashi wani irin qaimi da ya gigita hankalin dokin ya fita daga tsari da kuma horon da aka bashi. Yadda dokin yake misbehaving ya mugun tsoratata ya kuma daga mata hankali,ta sake riqeshi da dukka hannuwanta tana jin wani gumi yana tsarto mata,domin ta tabbatar a irin wannan yanayin ta sake ta fadi ba shakka sunanta gawa. Wani irin abu me nauyi ne taji ya saunar mata sanda dokinsa ya tsallakar iyakar dake tabbatar da kasantuwar nasara a hannunsa. Sautinsu amjad a amsa kuwwar da baisan inda aka samota ba da taken qasarsu ya sake ruda tunaninta da wani irin kalar zallar tashin hankali. Tayi zaton dokin zai dakata daga inda ya cimma wannan layin shima......amma aah sai ya zarce yaci gaba da shillawa da ita da wani irin gudun walqiya.....daidai da sunan data bashi. Wannan karon zuciyarta tsinkewa tayi gaba daya da wani irin tsoro,take ta fara gwada dukkan wasu dabaru ja tsaida doki a irin wannan yanayin. Dabararta ko daya batayi ba,firgici ya sake shigarta,tasan irin wannan yanayin idan doki ya shiga iya controlling dinsa sai Allah. Zuwa sannan hankulan mutane sun fara yowa kanta,musamman hadimanta da masu tsaronta wadanda suke da alhakin kula da lafiyarta. Sosai hankula sukayo kanta,al'ummarmu da son daukan abubuwa idan suka faru,da son ace sune suka fara dauka ko suka fara haskawa tuni suka fara nadar yadda abun yake kasancewa. Da wasu dawakan aka soma bin nata dokin da zummar shan gabansa,saidai hakan ya sake zama kamar wani qaimi suka bashi,don tunaninsa yana sake bashi anci gaba da wasanne......ana kuma son cimmasu,yanason cika umarnin uwar dakinsa ne kawai na tserewa duk wata halitta da zata wucesu,bama halittar doki dan uwansa kawai ba. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 33 ____________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ____________________________ Cak yayi a gurin yana kallon yadda suke bata kashi a tsakaninsu. Idanunsa ya dauke daga gurin,bacin ransa yana sake ninkuwa. Tseren doki da mace?,macen ma irin wannan da ba gama sanin yadda tsarin halittar dawakai da yadda ake hora doki da bashi umarni tayi ba?. "Kaje kace musu su tsaida dukkanin mutanen da suke binta" Haisam ya motsa labbansa yana furtawa omari dake tsaye kusa da dokinsa cikin bacin rai. Karon farko tun bayan wani lokaci da omari yaga shimfidadden bacin rai akan fuskar haisam din,sai ya juya a hankali cikin sanyin jiki yana nufar gurin masu bada sanarwa a wajen. "Kowa ya dakata!.....a dakata.....mahayan dawakai duka su fita a filin" Sanarwa data isa kunnuwansu kenan. Da yawansu abun bai musu dadi ba.....suna cike kuma da kokwanton yadda zasu bari dokin yaci gaba da galabaitar da ita. Wasu a cikinsu kuwa tuni sun fara hasashen irin tarin kadara da dukiyar da zasu mallaka sanadin tsaida wannan dokin. Tabbas sunsan cewa muddin ka zama silar tsiranta.......Allah ne kadai yasan daukakar da zaka samu a wajen sultane of agadez,don haka ba tare da abun ya musu dadi ba kowa ya janye abun hawansa daga filin,filin ya zamana ba kowa,daga dokin nata dake sake rikicewa,sai haisam da yayi tsaye saman nasa dokin yana dubanta. Idanuwa hankula da wayoyin dake tsakiyar filin suna nadar abinda ke faruwa Allah yayi yawa dasu. Da yawansu kuma sai suka maida daukar LIVE kai tsaye kenan daga hippodrome Niamey,wannan saqon ya bada notification a wayar tarin miliyoyi kuma dubbannin al'umma,kai tsaye kuma ya fada wayar falaak dake kwance cikin sofa tana qoqarin duba tafsirin wata aya a YouTube dinta,notification daga channel din SAUTI HIKIMA ya bayyana daga saman wayartata,sai kawai ta samu kanta da dannawa ta shiga ganin live video ne. Da fari bata fahimci komai ba,illa dai gudun da dokin yakeyi da matashiyar a samanta itama sai da taji ya tsinka mata Zuciya. Tana shirin sauka sunan yaja hankalinta. Princess khadeeja muhammad hammud(akhnan),sai kuma idanunta suka sauka akan comment da mutanen dake kan live din. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Falaak ta fadi tana fidda dukka idanunta cikin tsananin tsoro,sannan ta sauka daga saman sofa din da wani irin gaggawa tana qwalawa momma kira a gaggauce. Kusan kowa ya sare a wajen......yana ganin shima bazai iya tsaidashi ba,ganin yana tsaye kyam akan nashi dokin,ko saukowa baiyi ba. Wucewar farko ya bawa dokin wani sauti da ita kadai ta jishi,sautin da yafi kama da fito saidai ba fito bane.......ya sake wucewa a karo na biyu.......daya hangi yana shirin zagayawa karo na uku,sai ya saki linzamin nasa dokin ya diro daga samansa ya tsaya saman qafafunsa,ya riqe linzamin yana takawa dashi a hankali zuwa wannan iyakar yayi tsaye yana kallon yadda dokin yake tayar da qura yana nufoshi da gudun da ya rage da maganar daya masa dazu daga kaso dari cikin dari zuwa kaso saba'in cikin dari. Baya kadan yaja,sannan ya zube a qasa ya kafu akan gwiwoyinsa yana daga hannuwansa sama da wani irin yare da yasan ana tsaida dokunan hadaddiyar daular larabawa wato dubai. Duk da itace a saman dokin......duk da irin birkicewar data gama yi amma hakan bai hanata hasashen yadda nan da 'yan mintuna ko sakanni dokin nata zai murqesheshi yabi ta kansa ba. Tuna iya adadin yadda zai murjeshi ya canza masa kamanni kawai ya sanya tsigar jikinta zubawa. Wanne irin rawar kai ko tsautsayi koma dai tace qarar kwana ce zata sakashi tsaiwa haka gaban thunder a irin wannan yanayin?. Daidai imda tunaninta ya katse daidai sanda thunder din yaja wani irin birki daya kusa sakata fadowa ta gaba,bata kuma gama daidaituwa ba ya saki wata haniniya yana daga qafafuwansa na gaba sama,abinda ya sakata yin baya gaba daya ta tafi suuuu zata daki qasa. "Innalillahi wa 'inna ilaihi raji'un" Momma safiyya ta furta tana miqewa da wata irin razana......dukkan gabanta suka dauki rawa,zuciyarta na wani irin rawa itama kamar zata tsinke,yayin da falaak ta ruqunqume momma din da kyau wani irin tsoro yana cikata. Yayi imanin idan har ta fado a irin wannan yanayin ba abinda zai hana qashin qugunta tabuwa koma ta rasa lakarta gaba daya........yana matuqar qyamatar taba koda yatsar daba halal bace......amma kuma indai ya bari ta hadu da matsala daya cikin biyunnan ya tabbatar yana da nashi laifin a gurin Allah,wannan ya masa qaimi,cikin wata irin azama kar cirar walqiya ya isa gurin yana tokare kansa da qafarsa dake cikin boot,ya kuma miqa hannunsa guda daya ta fado akai,ta mirgina gaba daya ta fado jikinsa da wani irin matsanancin bugun zuciya daya bayyana a dukka gabanta da suke rawa. Iya qwayar idanunta kawai ya iya gani data fito ta tsakiyar helmet din kanta,ya zareta daga jikinsa da sauri yana tsaidata saman qafafunta gami da furta. "Astagfirullah wa'atubu ilaih" Da sautin daya tsaya iya saman labbansa,yanajin istigfarin yana zarcewa har cikin zuciyarsa. Tuni hadimanta suka fara bullowa da sauran ma'aikatan da hukumar wasan suna cika filin. A nutse yayi taku biyu baya sannan ya juya da zafin nama yana gyara zaman helmet dinsa yana takawa a zafafe da dukka kuzarinsa yana barin gurin. Duk takunsa daya idanunta yana kanshi.......duk da yawan jama'ar dake gabanta,wanda dukkaninsu sun iso ne su sake tabbatar da saukarta lafiya qalau. Kowanne taku nasa daya sai ya tada qura saboda karsashi da energy din da yake dashi,sannu a hankali har ya saje cikin dubbannin mutane ya bacewa ganinta. *MORSA* "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Shine abinda momma kawai taci gaba da maimaitawa ta kasa barin bakinta. Har yanzu hannunta yana dafe a qirjinta,har yanzu kuma tsananin bugun da zuciyarta keyi bai sassauta ba ko ya dakata,tashin hankalin da takeji kadan ya sauka,daga kashi dari zuwa casa'in. Me yakai akhnan jikin wani?.....me ma yakai akhnan filin tseren dawakai?,me ya sanyata a jerin 'yan wasa?,yaushe ta shiga?,yaushe ta fara?,bayan abubuwan da tasan tana yi a Niamey yaushe wannan din ya shiga cikin dabi'unta?. Har yanzu falaak na lafe a jikinta cikin matuqar tsoro,itama qirjinta bugawar kawai yakeyi har yanzu,gefe daya wasu siraran hawaye masu dumi suna sauka a hankali a kuncinta. Da gaske tana son 'yar uwarta......da gaske tana son biftu fiye da komai,tana da matsuguni me girma a zuciyarta,bata kuma sake gasgata hakan ba sai yanzu da wani mummunan abu ke daf da samunta. Batasan tana da girma da matsayi har haka a zuciyarta ba sai yanzu,shin menene a baya ya lullube girman wannan qaunar da take mata?,me yasa abaya bata fuskanci haka ba?. Rashin tashi da rayuwa qarqashin mahaifiya daya?,ko rashin rayuwa ne qarqashin kulawa iri daya?,ko nisan zango da tazarar dake tsakaninsu ya haifar da haka?. A mugun kasalance ta janye jikinta daga na momma din,sannan ta daga idanunta tana duban cikin idon momma. Maida kallonta itama momma din tayi a kanta,a nan falaak ta tsinci taruwar hawaye kwance cikin qwayar idanun momma din,wadda tayi murmushi wa falaak da zummar batar dasu,saidai maimakon su koma sai suka yiwa kansu hanya suka zubo. Sosai falaak taji wani irin tashin hankali ya yanko mata. Momma kuka?,yau momma ce da kuka?. Matar dake da wani irin dakakkiyar zuciya?,matar dake da wani irin juriya da jajircewa akan dukkan wahala ko tsanani?. "Momma....." Falaak ta fadi tana kai hannunta fuskar momma din. Riqe tsintsiyar hannun falaak tayi tana qin bari murmushin ya bace daga fuskarta. "Na kasa falaak......na kasa komai akan rayuwar akhnan......ina gani ina kallo a gabana rayuwarta take tabarbarewa a hankali a hankali da wani irin mataccen salo da zai qarasa maida rayuwarta abar qyama......na kasa falaak" Ta fada da wani irin mugun karaya. "Baki kasa ba momma......baki taba kasawa ba......a kullum ke din me nasara ce,a kullum cikin cin nasara kike kuma zakici gaba da cin nasara har abada......koda yaushe kina gayamin......akwai wani abu tattare da yaa biftu......akwai wani abu a rayuwarta......akwai abinda yake faruwa......su waye?.....meye a tattare da ita?" Falaak ta fada da mugun son jin komai a bayyana,kamar yadda ya zame mata dabi'a duk shekarun da suka shude.....tun daga shekarar da hankali ya fara zuwar mata zuwa yanzu,amsar da har yanzu batakai ga fahimtarta ba. Tsam momma ta miqe......har a ranta tana sake jin wata sabuwar qwarin gwiwa da iya kalaman falaak kawai.....kalaman da kullum suke shige dana hairaan,kalaman da sune kadai qwarin gwiwarta,sune kuma suke riqe da duk wani motsinta har kawo yanzu,har izuwa yau. "Akwai wani lokaci yana zuwa......akwai wani zamani tafe da za'ayi kyakkyawar farar walqiya.......a lokacin fuskokinsu da ayyukansu zasu bayyana.....inajin hakan a jikina falaak......amma me zai hana ne?,me kuma ya hana sultane tsaiwa a tsagina?.....ya tsaya a gefe na?" "Ni zan tayaki momma......ni zan tsaya a tsaginki" Falaak data dora hannunta a bayan mahaifiyarta ta fada,tana jin yaqinin da dukka zuciyarta kan abinda ta fada din. "Zan kusanci ya biftu kaman yadda kikeso.....zan samu kusanci da yaa akhnan kamar yadda kika tsara......zan zama a kusa da rayuwarta momma,na miki wannan alqawarin". A hankali a nutse kuma momma ta waiwayo tana duban falaak da dukka idanunta. Irin wannan nutsuwar......irin wannna kamalar....irin wannan dabi'un taso su zama rigar akhnan,irinsu taso ta siffantu dasu,koda falaak din ce zata kasance kamar akhnan a yanzu.....indai akhnan ta kasance kamar yadda falaak take a yanzun bata damu ba. (08187255862 lu'u lu'u paying) Jawo falaak tayi cikin jikinta tayi mata kyakkyawar runguma tana fadin "Allah yayi miki albarka......Allah ya hadamin kawunanku.......Allah ya baku dukkan kariya da tsari irin tasa". *AKHNAN* Runtse idanunta tayi tana me lafewa sosai cikin kujerun motar. Tun daga nan gurin.....tun kuma a sannan ta fara jin faduwa da muzanta sosai tana zagaye duk ilahirin jikinta. Daga sanda tayoyin motocinta suka fara dagawa suna barin gurin......mic din dake zagaye da gurin ya karade da sautin neman wanda yayi nasarar......kwatankwacin abinda ya faru a wancan satin da ita. First winner da suke kira a yanxu.....wanda da alama basu da cikakken sunansa,a wancan satin war haka sunanta ake kira......sunanta ne ya karade ilahirin amsa kuwwar ana nemanta a matsayin wadda tazo ta farko da gagarumar nasarar zubda maza sha daya,shin a yanzun meye ya canza wannan labarin?,meye ya canza wannan nasarar tata?.....WAYE SHI?. Wannan tambayar ita ta zame mata tambaya mafi muni kuma mafi barazana.......FADUWA RASHIN NASARA kalmomin da tafi tsana.....kalmomin da tayi nisan nesa dasu tsahon wasu shekaru yau gasu a kanta. Ta sani.....babu abinda zai canza wannan tarihin......babu abinda zai gogeshi.......babu abinda xai sauya sai idan har ta sake gwabza wani wasan ne tayi masa ninkin kayin da yayi mata. Ya cinye wasan......ya kuma zama shine wanda ya ceceta daga hannun thunder?,wanne irin asara ce wannan har haka a gareta?. Namiji ya kubutar da ita?,duk da tarin matan dake wajen?,bayan ya jawo mata asarar bacin suna?,anya kuwa har abada tana da maqiyi sama da wannan? Tafin hannunta takai kan dantsenta,har yanzu tana jin shati da alamun yatsunsa a gurin,har yanzu tana jin yatsunsa da irin tsautsarar riqon da yayi mata sanda take fadowa. Wani malolo yazo ya tokare mata a wuya,daga haihuwarta zuwa yanzu,babu wani d'a namiji da ya taba riqe koda farcenta ma bare yatsa ballantana kuma akai ga dantsenta. Sultane kadai.....sultane kawai a mazaunin mahaifinta shine ya taba samun wannan damar a dukka fadin rayuwarta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 34 ____________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ___________________________ An haifeta abar riritawa......abar yiwa tattali.....abar gatantawa da shagabawa,abu mafi girman daraja da tsada da agadez ke qunshe dashi.......wannan ya sanya ta zama abar kaffa kaffa da bawa kulawa. Ganinta koda a cikin gidan ma wani abune da ya zamana babbar sa'a ga duk wanda ya samu hakan.......bayan ta girma kuma,wannan jinin na sarauta ya fara motsawa a jikinta,wannan izzar isar taqamar da qasaitar da sarauta ke saukarwa ta sake mamaye jininta da kyau. A hankali ta fahimci irin tsadarta......ta gane darajarta,ta kuma karanci tattalin da ake mata,saita sake sawa ranta da gaske ita din ta musamman ce.....da gaske tasha bamban da dukka mata.....harta 'yar uwarta dake da daraja kwatankwacin tata wato FALAAK. Tana ji a ranta ita da falaak ba daya suke ba......akwai wasu tarin banbamce babance da darajoji data dara falaak din dashi nesa ba kusa ba. Tana jin a yau kamar ya barar da dukka wani wadannan darajoji da kima tata da wadannan laifukan guda biyu da yayi mata. Ta yaya zata barshi yaci bulus?,ya kamata ta bincika tasan koshi waye.......ya kamata ta fara hukuntashi ta kunyatashi ta hanyar bashi kayi kaman yadda yayi mata a gaban idanun mutane......kafin kuma tasa a masa mafi munin hukunci a bayan idanun kowa......a nesantashi da qasar da take rayuwa a cikinta. Abinda ke ranta yaqi wuce mata bare ta samu ta huta,har zuwa sanda ta zare kayan jikinta tsaf da takeji ta tsanesu ta bada umarnin a fita dasu,kada a sake dawo mata dasu cikin gidan,koda gilmawarsu bata qaunar ta sake gani,ta wuce zuwa bathroom dinta da yafi kama da wani parlor din alfarmar,ta wuce cikin jacuzzi ta sakarwa kanta ruwa me bala'in dumin da kadan ya rage yayi zafi sosai. Batasan adadin awannin data dauka cikin ruwan ba yana saukar mata tsakiyar kanta ba. Idanunta kan ruwan dake gudu ta rariyar,tana jin inama wannan ranar ta wuce da dukka wani memory na dukka al'ummar da suke wajen abun ya faru?,inama ace zata iya shafe komai ta mantar da kowa komai ya wuce tamkar bai faru a ranar ba?. Dukka hannuwanta ta saka tana maida jiqaqqiyar sumarta baya,wadda ta lafe saman farar fatarta tsahonta yana kaiwa dab da mazaunanta. Iska ta furzar daga bakinta ta cikin ruwan,tana tuna yadda ya tureta daga jikinsa ya kuma direta saman qafafunta. Batasan sanda hawaye ya balle mata ba,kamar ita?......diya guda ga sultane.......akhnan muhammad?......har wani ya samu damar kusanci da jikinta?......har yana jin ta zame masa damuwar da zai tureta har haka?. Wata mahaukaciyar tsanarsa ta taso mata......ta kuma yi mata tsaye a zuciyarta ta sakata sakin kuka sosai cikin ruwan. Dama can ya shirya komai ne......dama can ya shirya faruwar hakan......banda haka ta yaya tana zaman zamanta yayi requesting yayi tsere da ita?,ita daya tallin tal!....duk tarin 'yan wasan da Niamey dama niger gaba daya take dasu?. Batasan ta dauki lokaci me tsaho a bandakin ba sai da taji Shehinaz na knocking qofar daga waje,ta ciri wani siririn band ta daure gashinta sannan ta fito ta sabe jikinta ta koma cikin bathtub ta qarasa wankan. Sanda ta fito da aisa da Shehinaz dukkaninsu suna zaune a mabanbantan gurare cikin dakin. Kowacce waya ce a hannunta,ba wannan hirar ba kuma karadin. Da kanta ta sake yiwa kanta alqalanci.......tunda har a yau takejin nauyi da wani irin rashin dadi cikin ranta tsakaninta dasu aisa.....su aisa din da kafin mallakar hankulansu hatta da wanda suna iya shiga bandaki daya kat kenan......amma a yau takejin nauyin kallon idanunsa?. Cikin dukkanin jikinta gaba daya take jin ta muzanta......cikin kowanne motsawa da zatayi ji take kaman aisa da Shehinaz suna kallonta ne......kamar suna mata kallon marar sa'a!......mara nasara!...... Da wannan tunanin ta sauya kayan da birra ta ajiye mata. Lumshe ido tayi tana shaqar wani qamshi na daban da taji yau kayan sukeyi. Lallausan qamshin nan na musamman daga turaren incense by kabo daughter(+234 803 211 9803 tasted and trusted). Kawai aisa ta gwada yi mata kabbasar kayanne......sanin kyakkyawar alaqa da soyayyarta da qamshi,wataqila hakan zai sanyaya mata zuciyarta. Ta samu nutsuwa sosai cikin sallarta,kamar yadda qamshin ya huda zuciyarta sosai ya soma rage radadin da takeji. Saidai sanda ta kammala sallar komawa tayi ta lafe cikin sofa tana nannade jikinta da kyau cikin after dress din me yalwa da tayi sallar da ita,ta kuma maida idonta ta rufe ruf ba tare da tace da kowa komai ba,tana shaqar lallausan qamshin kabbasar a hankali tana tattaro nutsuwarta. Ganin haka ya sanya aisa qyarawa Shehinaz,sai kawai suka miqe a nutse suna ficewa a dakin gami da ja mata qofar kowa baice komai da ita ba. ★★ *HAISAM*★★ Daga yadda shirunsa ya kasance tun bayan sallama da yayi dasu khadeem bayan ya jagorancesu sallar magariba sannan sukayi sallama suka wuce filin sauka da tashi jiragen sama na Niamey din omari ya gama sanin an samu matsala. Daga yanayin idanunsa kadai omari ya fahimci ranshi a tsananin bace yake,wani irin mutum ne shi da sam ba kasafai ya fiya magana ba koda ba cikin fushi yake ba ballantana yana cikin fushi. Yayi riqo sosai da hadith dinnan na ma'aiki S A W da yayi hani da magana cikin fushi,idan kana tsaye kuma ka zauna. Zai iya qayyade sau nawa ya taba ganinsa yana magana alhalin cikin fushi yake?. A karo na barkatai omari ya sake dubansa. Ya sauya kayansa zuwa wasu Indonesian kurta farare tas masu laushi,wadanda aka yiwa ado da gray color din zare. Kanshi ba hula sai tattausan gashinsa dake a gyare tsaf.....kai bakace shine wannan da yayi tsere awa biyu baya da suka wuce ba. Jikinsa da lallausan turaren nan nasa ya zaunawa qamshinsa ne yake fita a hankali da wani irin sanyi me kwantar da rai. Dan qaramin littafi ne a hannunsa da tunda suka zauna a motar shi yake dubawa shafi shafi. Wannan din na cikin dabi'arsa ta biyu. Indai ranshi yana a bace ba abinda yake bashi peace da relief sai karatu. Yana iya gamawa da littafi guda idan yana cikin fushin da baison a matsa masa yayi magana duk yawan mas hafin littafin. Yaso qwarai kada yace masa komai kamar yadda aikinsa ya nuna buqatarsa kenan,to amma kuma ya gaji da canki cankin ganin sun dauki hanya d'od'ar,su da suke da ticket na jirgin da zai sauka agadez qarfe bakwai da rabi na safiyar washegari. Bugu da qari driver din dake tuqasu a yanzu dan qasar ne,ba baqo bane irinsu ballantana yayi tunanin bace hanya yayi. "Amma fa.....kamar awa guda kawai ya ragewa jirginmu ya tashi.....kuma naga mp din yana nuna mun dauki hanyar barin Niamey ne". Omari ya furta a nutse kaman bashi ba. Sau tari fushin haisam baya bayyana muraran,amma su suna kalla suke ganewa. Dukkaninsu suna shiga wani sabon hankali da sabuwar nutsuwar idan ran haisam ya baci,bawai don zai gaya musu maganganu marasa dadi,ko zaiyi fada da dayansu ba....aah.....sai don nauyinsa da sukeji da wani irin kwarjini da nutsuwa da Allah ya bashi. Zai qalubalanceka ne idan buqatar hakan ta kama da wani irin nutsuwa da hikima a kalamansa......zai kuma dafaka da ruwan jikinka idan baikai yace komai da kai ba. Ba tare daya dauke littafin a fuskarsa ba ko ya dubi omari ba ya amsa masa. "Buqatar tafiya a motar tafi ta tafiya a flight muhimmanci" Ya amsa a taqaice yana buda shafin gaba na littafinsa. Shuru omari yayi yana sake zuba masa idanu. Wato halin zai gwada masa a aikace?.....shikam baya jurar wannan,bazai bari bama su shiga garin mutane da basusan komai nasu ba da wannan halin da haisam ya yanke nuna masa. "Amma dukka wannan shariyar ta mece?,da magana a cikinka mafi kyau ka fito ka fadeta" Omari ya fada cikin nashi kalar iya rigimar yana hade rai da bata fuska kaman shi akawa laifin. Bai kalleshi ba,amma yadda yayi maganar kadai haisam yasan me yake shirin yi,don haka yayi kaman baiji me yake cewa ba. Bai magantun ba kuwa har sai da omari ya fidda rai zaice wani abu din,sannan ya rufe littafin a nutse bayan ya saka alama ya ajjiyeshi daga gefansa. "Me kakeso nace maka omari?.......ince maka ka kyauta daka hadani tsere da wadda take ba muharramata ba?......ko ince maka kyauta daga sakani hada jiki da matar da take haramun nayi mata koda zuzzurfan kallo ballanta jikkunanmu su hadu?.....ko kuma nace maka ka kyauta data sanadinka d'iyar mutane ta kusa ransa lafiyarta ko ranta?". Idanu omari ya fidda yana duban haisam. "Me kake cewa ne?....." Hannu haisam ya daga masa calmly yana lumshe idanunsa gami da budesu akansa. "Karka musa akan komai.....zanta istigar......nasan Allah da zuciya yake amfani......amma zamuyi aiki dakai ne omari a bisa sharuddan da idan ba zaka iya kiyayesu ba.......zaka fita daga cikin deal dinnan......ina magana ne a matsayin boss dinka....a yanzu...a wannan lokacin.......not your friend?" Ya qarashe da sigar tambaya yana kallon idanun omari. Idon haisam kadai ya gaya masa muhimmancin daya dauki aikin dashi. A komai haisam me sauqin fahimta ne,me kuma bada uzuri ne banda akan aikinsa. Zaiyiwa haisam uzuri sau million times idan har yanason hakan.....don yasan wayeshi a waje a kuma bayan aikinsa. "Yes sir" Omari ya fada da dukka girmamawa da seriousness. ★Yadda ta farka a firgice shi ya sanya aisa dake daura dankwalinta gaban madubi tsorata itama. Sosai ta maida dubanta ga akhnan da farkawarta kenan a baccin. (08187255862 lu'u lu'u paying) Zama tayi sosai cikin kujerar tana saka fuskarta a tafin hannunta ba tare data damu da gyaran hargitsatsen gashin kanta ba. Ajiyar zuciya aisa ta sauke tana maida hankalinta ga abinda takeyi cikin madubin. Tsakanin jiya da yau mafarkinta na uku kenan. Mafarkin data gama fahimtar ba akan komai bane sai akan abinda ya faru jiyan. "Ya kamata ki sassautawa kanki haka,abinda ya faru ya riga ya faru,saidai kuma a kiyaye gaba" Aisa ta fadi hankalinta kwance. Ko kadan batajin zatayi tarayya da akhnan wajen tayata jin ciwon abinda ya faru da ita,komai daya farun tana dangantashi da zallar rashin jin magana da shawarar irin nasu ita da Shehinaz. Inda ta dauka shawararta,inda taji abinda ta fada mata for the first place ma da ba'azo nan din ba. "Na wuce office......na bayar da sanarwar baki da lafiya don kada office dinki ya zama ba wani motsi......yana da kyau ki qwarara jikinki ki koma office dinki" Aisa ta fada tana yin gaba gami da ficewa daga dakin. Da fari hawaye take zubarwa,amma maganganun aisa sai suka sake saka mata dafi a ranta. Da gaske ya cuceta ya tsaida komai nata. Walwalarta,nishadinta dama ayyukanta. Hakan kuma bai isa ba,har cikin baccin da take samun salama shima bai barta ba?. Wanne irin mutum ne shi?,wanne irin azzalumi ne?,anya ruhinta zai samu salama kuwa idan bata rama abinda yayi mata ba?. Kuka me qaramin sauti ta saki ta jawo pillow tana kwantar da kanta gami da maida gashinta baya. Daidai sanda aisa ta dawo don ta manta tabar wayarta cikin dakin. Wani mamaki ne ya sauko ya lullubeta ganin kukan da akhnan keyi,kuma ganinta bai sanyata ta dakatar da kukan ta ba. Bawai bata yin kuka bane.....a'ah.....hasalima ita din irin mutanen nan ne da abun kuka baya masu kadan,don ko a quruciyarsu a rana tayi kuka kadan tayi biyar zuwa bakwai,to amma tunda ta zama cikakkiyar mace waye ma zai bata ranta ballantana ya sakata kuka?.....ko na quruciyar ma da tayi ta yishi ne saboda yarinta da kuma dabi'a. Ta manta rabon da taga akhnan din tana kuka,abun sai ya zame mata wani baqon abu. Cikin zuciyarta ta sake tabbatarwa,tunda har hawaye ya zuba daga idanun akhnan din lallai abun babba ne a zuciyarta. Ta rasa yadda zatayi controlling dinta dole ta kira Shehinaz,saidai ko ita dinma akhnan bata saurara ba. Zafin da takeji a zuciyarta tana jin bashi da hanyar samun sassauci na farko irin su barta tayi kukan. Mamaki yaqi barin aisa. Princess dinnan ta agadez?.....CEO ta sahel couture guda ta zauna tana kuka akan wani abu da a wajenta baida wannan girman?,to wai quruciya ce har yanzu a jikin akhnan ko kuma zallar radadi da k'i fadin ne yake taba zuciyarta?. Duk yadda suka dauki abun da sauqi ita da Shehinaz sai suka lura sama da haka akhnan ta daukeshi. Wunin guda tana qunci,tsakanin aisa da Shehinaz dinma daga qarshe ba wanda ya fita office din. *8:00 pm* Yadda sultanate ya zubawa wayar idanu yana kallon abinda ke wakana haka itama morsa safiyya ta kafeshi da kaifafan idanunta tana kallon kowanne reaction nasa a duk gilmawar video din. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 34 ____________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ___________________________ An haifeta abar riritawa......abar yiwa tattali.....abar gatantawa da shagabawa,abu mafi girman daraja da tsada da agadez ke qunshe dashi.......wannan ya sanya ta zama abar kaffa kaffa da bawa kulawa. Ganinta koda a cikin gidan ma wani abune da ya zamana babbar sa'a ga duk wanda ya samu hakan.......bayan ta girma kuma,wannan jinin na sarauta ya fara motsawa a jikinta,wannan izzar isar taqamar da qasaitar da sarauta ke saukarwa ta sake mamaye jininta da kyau. A hankali ta fahimci irin tsadarta......ta gane darajarta,ta kuma karanci tattalin da ake mata,saita sake sawa ranta da gaske ita din ta musamman ce.....da gaske tasha bamban da dukka mata.....harta 'yar uwarta dake da daraja kwatankwacin tata wato FALAAK. Tana ji a ranta ita da falaak ba daya suke ba......akwai wasu tarin banbamce babance da darajoji data dara falaak din dashi nesa ba kusa ba. Tana jin a yau kamar ya barar da dukka wani wadannan darajoji da kima tata da wadannan laifukan guda biyu da yayi mata. Ta yaya zata barshi yaci bulus?,ya kamata ta bincika tasan koshi waye.......ya kamata ta fara hukuntashi ta kunyatashi ta hanyar bashi kayi kaman yadda yayi mata a gaban idanun mutane......kafin kuma tasa a masa mafi munin hukunci a bayan idanun kowa......a nesantashi da qasar da take rayuwa a cikinta. Abinda ke ranta yaqi wuce mata bare ta samu ta huta,har zuwa sanda ta zare kayan jikinta tsaf da takeji ta tsanesu ta bada umarnin a fita dasu,kada a sake dawo mata dasu cikin gidan,koda gilmawarsu bata qaunar ta sake gani,ta wuce zuwa bathroom dinta da yafi kama da wani parlor din alfarmar,ta wuce cikin jacuzzi ta sakarwa kanta ruwa me bala'in dumin da kadan ya rage yayi zafi sosai. Batasan adadin awannin data dauka cikin ruwan ba yana saukar mata tsakiyar kanta ba. Idanunta kan ruwan dake gudu ta rariyar,tana jin inama wannan ranar ta wuce da dukka wani memory na dukka al'ummar da suke wajen abun ya faru?,inama ace zata iya shafe komai ta mantar da kowa komai ya wuce tamkar bai faru a ranar ba?. Dukka hannuwanta ta saka tana maida jiqaqqiyar sumarta baya,wadda ta lafe saman farar fatarta tsahonta yana kaiwa dab da mazaunanta. Iska ta furzar daga bakinta ta cikin ruwan,tana tuna yadda ya tureta daga jikinsa ya kuma direta saman qafafunta. Batasan sanda hawaye ya balle mata ba,kamar ita?......diya guda ga sultane.......akhnan muhammad?......har wani ya samu damar kusanci da jikinta?......har yana jin ta zame masa damuwar da zai tureta har haka?. Wata mahaukaciyar tsanarsa ta taso mata......ta kuma yi mata tsaye a zuciyarta ta sakata sakin kuka sosai cikin ruwan. Dama can ya shirya komai ne......dama can ya shirya faruwar hakan......banda haka ta yaya tana zaman zamanta yayi requesting yayi tsere da ita?,ita daya tallin tal!....duk tarin 'yan wasan da Niamey dama niger gaba daya take dasu?. Batasan ta dauki lokaci me tsaho a bandakin ba sai da taji Shehinaz na knocking qofar daga waje,ta ciri wani siririn band ta daure gashinta sannan ta fito ta sabe jikinta ta koma cikin bathtub ta qarasa wankan. Sanda ta fito da aisa da Shehinaz dukkaninsu suna zaune a mabanbantan gurare cikin dakin. Kowacce waya ce a hannunta,ba wannan hirar ba kuma karadin. Da kanta ta sake yiwa kanta alqalanci.......tunda har a yau takejin nauyi da wani irin rashin dadi cikin ranta tsakaninta dasu aisa.....su aisa din da kafin mallakar hankulansu hatta da wanda suna iya shiga bandaki daya kat kenan......amma a yau takejin nauyin kallon idanunsa?. Cikin dukkanin jikinta gaba daya take jin ta muzanta......cikin kowanne motsawa da zatayi ji take kaman aisa da Shehinaz suna kallonta ne......kamar suna mata kallon marar sa'a!......mara nasara!...... Da wannan tunanin ta sauya kayan da birra ta ajiye mata. Lumshe ido tayi tana shaqar wani qamshi na daban da taji yau kayan sukeyi. Lallausan qamshin nan na musamman daga turaren incense by kabo daughter(+234 803 211 9803 tasted and trusted). Kawai aisa ta gwada yi mata kabbasar kayanne......sanin kyakkyawar alaqa da soyayyarta da qamshi,wataqila hakan zai sanyaya mata zuciyarta. Ta samu nutsuwa sosai cikin sallarta,kamar yadda qamshin ya huda zuciyarta sosai ya soma rage radadin da takeji. Saidai sanda ta kammala sallar komawa tayi ta lafe cikin sofa tana nannade jikinta da kyau cikin after dress din me yalwa da tayi sallar da ita,ta kuma maida idonta ta rufe ruf ba tare da tace da kowa komai ba,tana shaqar lallausan qamshin kabbasar a hankali tana tattaro nutsuwarta. Ganin haka ya sanya aisa qyarawa Shehinaz,sai kawai suka miqe a nutse suna ficewa a dakin gami da ja mata qofar kowa baice komai da ita ba. ★★ *HAISAM*★★ Daga yadda shirunsa ya kasance tun bayan sallama da yayi dasu khadeem bayan ya jagorancesu sallar magariba sannan sukayi sallama suka wuce filin sauka da tashi jiragen sama na Niamey din omari ya gama sanin an samu matsala. Daga yanayin idanunsa kadai omari ya fahimci ranshi a tsananin bace yake,wani irin mutum ne shi da sam ba kasafai ya fiya magana ba koda ba cikin fushi yake ba ballantana yana cikin fushi. Yayi riqo sosai da hadith dinnan na ma'aiki S A W da yayi hani da magana cikin fushi,idan kana tsaye kuma ka zauna. Zai iya qayyade sau nawa ya taba ganinsa yana magana alhalin cikin fushi yake?. A karo na barkatai omari ya sake dubansa. Ya sauya kayansa zuwa wasu Indonesian kurta farare tas masu laushi,wadanda aka yiwa ado da gray color din zare. Kanshi ba hula sai tattausan gashinsa dake a gyare tsaf.....kai bakace shine wannan da yayi tsere awa biyu baya da suka wuce ba. Jikinsa da lallausan turaren nan nasa ya zaunawa qamshinsa ne yake fita a hankali da wani irin sanyi me kwantar da rai. Dan qaramin littafi ne a hannunsa da tunda suka zauna a motar shi yake dubawa shafi shafi. Wannan din na cikin dabi'arsa ta biyu. Indai ranshi yana a bace ba abinda yake bashi peace da relief sai karatu. Yana iya gamawa da littafi guda idan yana cikin fushin da baison a matsa masa yayi magana duk yawan mas hafin littafin. Yaso qwarai kada yace masa komai kamar yadda aikinsa ya nuna buqatarsa kenan,to amma kuma ya gaji da canki cankin ganin sun dauki hanya d'od'ar,su da suke da ticket na jirgin da zai sauka agadez qarfe bakwai da rabi na safiyar washegari. Bugu da qari driver din dake tuqasu a yanzu dan qasar ne,ba baqo bane irinsu ballantana yayi tunanin bace hanya yayi. "Amma fa.....kamar awa guda kawai ya ragewa jirginmu ya tashi.....kuma naga mp din yana nuna mun dauki hanyar barin Niamey ne". Omari ya furta a nutse kaman bashi ba. Sau tari fushin haisam baya bayyana muraran,amma su suna kalla suke ganewa. Dukkaninsu suna shiga wani sabon hankali da sabuwar nutsuwar idan ran haisam ya baci,bawai don zai gaya musu maganganu marasa dadi,ko zaiyi fada da dayansu ba....aah.....sai don nauyinsa da sukeji da wani irin kwarjini da nutsuwa da Allah ya bashi. Zai qalubalanceka ne idan buqatar hakan ta kama da wani irin nutsuwa da hikima a kalamansa......zai kuma dafaka da ruwan jikinka idan baikai yace komai da kai ba. Ba tare daya dauke littafin a fuskarsa ba ko ya dubi omari ba ya amsa masa. "Buqatar tafiya a motar tafi ta tafiya a flight muhimmanci" Ya amsa a taqaice yana buda shafin gaba na littafinsa. Shuru omari yayi yana sake zuba masa idanu. Wato halin zai gwada masa a aikace?.....shikam baya jurar wannan,bazai bari bama su shiga garin mutane da basusan komai nasu ba da wannan halin da haisam ya yanke nuna masa. "Amma dukka wannan shariyar ta mece?,da magana a cikinka mafi kyau ka fito ka fadeta" Omari ya fada cikin nashi kalar iya rigimar yana hade rai da bata fuska kaman shi akawa laifin. Bai kalleshi ba,amma yadda yayi maganar kadai haisam yasan me yake shirin yi,don haka yayi kaman baiji me yake cewa ba. Bai magantun ba kuwa har sai da omari ya fidda rai zaice wani abu din,sannan ya rufe littafin a nutse bayan ya saka alama ya ajjiyeshi daga gefansa. "Me kakeso nace maka omari?.......ince maka ka kyauta daka hadani tsere da wadda take ba muharramata ba?......ko ince maka kyauta daga sakani hada jiki da matar da take haramun nayi mata koda zuzzurfan kallo ballanta jikkunanmu su hadu?.....ko kuma nace maka ka kyauta data sanadinka d'iyar mutane ta kusa ransa lafiyarta ko ranta?". Idanu omari ya fidda yana duban haisam. "Me kake cewa ne?....." Hannu haisam ya daga masa calmly yana lumshe idanunsa gami da budesu akansa. "Karka musa akan komai.....zanta istigar......nasan Allah da zuciya yake amfani......amma zamuyi aiki dakai ne omari a bisa sharuddan da idan ba zaka iya kiyayesu ba.......zaka fita daga cikin deal dinnan......ina magana ne a matsayin boss dinka....a yanzu...a wannan lokacin.......not your friend?" Ya qarashe da sigar tambaya yana kallon idanun omari. Idon haisam kadai ya gaya masa muhimmancin daya dauki aikin dashi. A komai haisam me sauqin fahimta ne,me kuma bada uzuri ne banda akan aikinsa. Zaiyiwa haisam uzuri sau million times idan har yanason hakan.....don yasan wayeshi a waje a kuma bayan aikinsa. "Yes sir" Omari ya fada da dukka girmamawa da seriousness. ★Yadda ta farka a firgice shi ya sanya aisa dake daura dankwalinta gaban madubi tsorata itama. Sosai ta maida dubanta ga akhnan da farkawarta kenan a baccin. (08187255862 lu'u lu'u paying) Zama tayi sosai cikin kujerar tana saka fuskarta a tafin hannunta ba tare data damu da gyaran hargitsatsen gashin kanta ba. Ajiyar zuciya aisa ta sauke tana maida hankalinta ga abinda takeyi cikin madubin. Tsakanin jiya da yau mafarkinta na uku kenan. Mafarkin data gama fahimtar ba akan komai bane sai akan abinda ya faru jiyan. "Ya kamata ki sassautawa kanki haka,abinda ya faru ya riga ya faru,saidai kuma a kiyaye gaba" Aisa ta fadi hankalinta kwance. Ko kadan batajin zatayi tarayya da akhnan wajen tayata jin ciwon abinda ya faru da ita,komai daya farun tana dangantashi da zallar rashin jin magana da shawarar irin nasu ita da Shehinaz. Inda ta dauka shawararta,inda taji abinda ta fada mata for the first place ma da ba'azo nan din ba. "Na wuce office......na bayar da sanarwar baki da lafiya don kada office dinki ya zama ba wani motsi......yana da kyau ki qwarara jikinki ki koma office dinki" Aisa ta fada tana yin gaba gami da ficewa daga dakin. Da fari hawaye take zubarwa,amma maganganun aisa sai suka sake saka mata dafi a ranta. Da gaske ya cuceta ya tsaida komai nata. Walwalarta,nishadinta dama ayyukanta. Hakan kuma bai isa ba,har cikin baccin da take samun salama shima bai barta ba?. Wanne irin mutum ne shi?,wanne irin azzalumi ne?,anya ruhinta zai samu salama kuwa idan bata rama abinda yayi mata ba?. Kuka me qaramin sauti ta saki ta jawo pillow tana kwantar da kanta gami da maida gashinta baya. Daidai sanda aisa ta dawo don ta manta tabar wayarta cikin dakin. Wani mamaki ne ya sauko ya lullubeta ganin kukan da akhnan keyi,kuma ganinta bai sanyata ta dakatar da kukan ta ba. Bawai bata yin kuka bane.....a'ah.....hasalima ita din irin mutanen nan ne da abun kuka baya masu kadan,don ko a quruciyarsu a rana tayi kuka kadan tayi biyar zuwa bakwai,to amma tunda ta zama cikakkiyar mace waye ma zai bata ranta ballantana ya sakata kuka?.....ko na quruciyar ma da tayi ta yishi ne saboda yarinta da kuma dabi'a. Ta manta rabon da taga akhnan din tana kuka,abun sai ya zame mata wani baqon abu. Cikin zuciyarta ta sake tabbatarwa,tunda har hawaye ya zuba daga idanun akhnan din lallai abun babba ne a zuciyarta. Ta rasa yadda zatayi controlling dinta dole ta kira Shehinaz,saidai ko ita dinma akhnan bata saurara ba. Zafin da takeji a zuciyarta tana jin bashi da hanyar samun sassauci na farko irin su barta tayi kukan. Mamaki yaqi barin aisa. Princess dinnan ta agadez?.....CEO ta sahel couture guda ta zauna tana kuka akan wani abu da a wajenta baida wannan girman?,to wai quruciya ce har yanzu a jikin akhnan ko kuma zallar radadi da k'i fadin ne yake taba zuciyarta?. Duk yadda suka dauki abun da sauqi ita da Shehinaz sai suka lura sama da haka akhnan ta daukeshi. Wunin guda tana qunci,tsakanin aisa da Shehinaz dinma daga qarshe ba wanda ya fita office din. *8:00 pm* Yadda sultanate ya zubawa wayar idanu yana kallon abinda ke wakana haka itama morsa safiyya ta kafeshi da kaifafan idanunta tana kallon kowanne reaction nasa a duk gilmawar video din. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 36 ___________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ____________________________ "Na shiga uku!" Ta furta a fili tana cusa yatsunta cikin gashin kanta dake hargitse tana maidashi baya. Ita kanta a yanzun data kalli gurin,ta kuma sakashi a mizanin hasashen gata ga sultane suke kalla......mene zai iya faruwa?". "Biftu......Calme-toi! Uhmnn(ki kwantar da hankalinki uhmm)" "Shehinaz......sultane ne fa da kanshi ya kirani......bana ji a jikina lafiya ko dadi ne suka sa hakan......kira da kuma umarni dukka na kai tsaye?" Tayi maganar idanunta na nuna tabata da abun yayi. "Détends-toi!,(ki nutsu),Qu'est-ce qu'il a dit exactement?(me yace miki?)" Numfashi taja sosai,tana son tsoron da takeji yana task masa ya narke da kansa,a nutse ta motsa labbanta. "Kome da nake na bari,alhamis tayimin a agadez,akwai abu me muhimmanci a ranar juma'a". Shuru shehinaz tayi,ita kanta tasan lallai tabbas akwai wani magana a qasa,banda hakan sultane bai taba yi musu ko yiwa akhnan zabin ranar zuwanta agadez ko ranar barinta ba. "Calme-toi,il ne va rien se passer,khairan in sha Allah(ki kwantar da hankalinki......babu abinda zai faru,khairan in sha Allah". Shehinaz ta fada tana sake son gamsar da akhnan din cewa ba wani abu din bane. *_AGADEZ_* Batayi ajiyar komai cikin ranta ba saboda samun tabbacin ta kafawa sultane qusar da zai wahala akhnan ta cireta.....zai wahala wannan karon tarin soyayyar da yake mata......tarin qauna da riritawar yayi tasirin kasa daukar matakin daya dace cikin rayuwarta. Don haka hankali kwance ta isa farfajiyar da takan zauna a duk yammaci irin wannan. Kusan idan tayi irin wannan zaman,zama ne na musamman saboda al'ummar agadez......takan zauna ne don sauraren koken al'umma,wanda asma'u mataimakiyarta ta musamman data ajiye saboda sauraren koke da damuwar jama'ar masarautar dama na wajenta. Buqatu na mutane birjik da damuwoyinsu data maida nata. Cikin kudinta,cikin arziqin da Allah ya hore mata. Sam bata taba gajiyawa ko kuma kasawa ba koda sau daya. Kunnuwanta suna kan asama'u dake lissafosu daki daki,yayin da take matsa carbin hannunta a nutse zuciyarta kuma tayi nisa karanta "subhanallahi wabi hamdihi,subhanallahil azeem" (Kalmomi ne da Allah yake sonsu,suke kuma nauyaya ma'aunin aikin bayi ranar awon ayyuka). Muryar aeera ta jiyo daga inda take ita da Aafreen,kafin daga bisani ta hangi falaak na tahowa,hannunta dauke da qur'anin Aafreen. Jikin momma aeera ta fada tana bata labarin ta haddace karatunta na jiya har an qara mata wani. Murmushin momma ta saki,a duk sanda ta gansu suna tafiya ko dawowa daga daukan karatun,tana jin wani nutsuwa gami da aminci har qasan ranta,tana jin wani kwanciyar hankali yana saukar mata. "Momma.....malam yace yana buqatar magana dake idan an masa izini". Aafreen ta fada tana zama kan daya daga cikin tuntum din da aka qawata wajen dashi saboda hutawa. Sai data kalli falaak ta gyada mata kai alamun haka ne,sannan ta dakatar da asama'u. "Ayi masa iso" Tace da asama'u tana gyara zamanta gami da sake lullube ilahirin jikinta da kyau. Cikin qasa da mintuna goma ya bayyana a wajen. Cikin shigar manyan kaya na wani tattausan yadi babbar riga da 'yar ciki. Akwai kamala da nutsuwa sosai tare dashi,shekarunsa na haihuwa zasu kai aqalla arba'in da biyar zuwa da takwas. Cikin karramawa tasa aka tarbeshi,kafin su fara magana. "Da dadewa na cike foam na ummul_quraa a madeena......shekara guda kenan sai wannan satin Allah yayi na samu sanarwar samun gurbin karatu acan din,wannan dalilin ya sanya nace bari na sanar miki.....ina me bada haquri mun fara karatu da yara kuma zai yanke". Sosai momma taji zuwan maganar a wani abu na ba zata,har cikin ranta taji sam labarin bai mata dadi ba,to amma ci gaba ne ya samu malam Ousmane haris din,koda akan kanta ne ko yaranta kuma hakan zata kalleshi a abun alkhairi. "Ma sha Allah malam.....na tayaka murna sosai.....ci gaba ne da qaruwa ai,ba kuma akanmu kawai ba.....har qasarmu gaba daya,Allah yasa albarka". "Ameen,godiya nake". "Ma sha Allah.....in sha Allahu zan aika da tawa gudunmawar tafiyar". Murmushi ya danyi "To Allah ya saka da alkhairi" "Ameen ameen......saidai kuma wani hanzari ba gudu ba......karatun yaran nan,banaso ya tsaya malam......don Allah idan ba damuwa.....ko zaka duban wani amintacce cikin amintattunka?". Shuru kadan yayi na wasu daqiqu kafin ya nisa. "Mutum daya ne na amince dashi,nasan kuma zai iya fiye ma da abinda zanyi,don iliminsa ya zarga nawa nesa ba kusa ba.....saidai kuma shi din mutum ne me wuyar sha'ani,hasalima bani da tabbas din zaiyi,kinga kuwa baima kamata na bada sunansa ba". Tashin farko momma taji maganganun malam Ousmane haris ya zauna a ranta,karon farko kuma hankalinta taji ya zauna daidai kan wanda taji yana yiwa yabon da kuma tabbacin samun karatu sama da wanda shi yake bawa yaran. "Don Allah malam.....ko za'a roqa mana ALFARMARSA?......ko nawa ne zan biyashi......ya daure yaci gaba da dukan nauyin karatun yarannan". Shuru malam Ousmane haris yayi,kafin daga bisani ya sauke ajiyar zuciya. " Abinda za'a biyashi ba shine damuwar ba,ku din da yaran,na tabbatar sai ya saka ya kuma kafa musu wasu qa'idoji da dokoki muddin zai daukesu karatu,ban sani ba ko zaku iya jure hakan Allah ya taimakeki". Qaramin murmushi momma ta saki tana daidaita zamanta. "Banda abun malam Ousmane......ai nafison irin wannan tsarin koyarwar......kuma ina son mu'amala da irin wadannan mutanen,don nasan cewa komai nasu in sha Allah zai zamana a nutse ne bisa tsari......wannan aikin za'a yimin malam.....ya fadi duka tsare tsarensa.....in sha Allah zasu kiyaye". Qasa malam Ousmane haris yayi da kansa. Yana jin nauyin matar qwarai,saboda tarin alkhairanta da sanin ya kamata da take dashi. "In sha Allah komai zai zo da sauqi". "Momma" Falaak ta kirata sanda take shirin maida hankalinta ga asama'u bayan sun kammala da Ousmane haris. Duban falaak din tayi,ta bata fuska sosai "Gani nakeyi ba malamin da zaizo da yafi malam iya koyarwa.....na dauka zaki hana mishi tafiyar ne saboda karatunmu". Murmushi kadan momma tayi,sai ta ajiye takardar da asama'u ta miqa mata zata duba tana kallon falaak din. "Bakisan duk me hankali yana mu'amalantar malami tamkar sarki ba saboda girman qur'ani da tarin alfamar littatafan da suke kanshi ba......abune da bai dace ba kayi karantsaye cikin al'umaransu ba........suna da daraja da martaba sama da wadda sarakuna da masu mulki suke da ita......baka da hurumin amfani da qarfin iko ko na mulkinka na sanyasu yin abinda basuji amincinsa a zuciyarsu ba.....tsakaninka dasu biyayya girmamawa da tausasawa". Kai falaak ke gyadawa tana sake samum gamsuwa da dukka bayanan momma din. Ita din shaida ce,taga wasu irin mabanbantan dabi'u masu kyau da nagarta gami da burgewa tattare da malam Ousmane haris da bata zaci akwai sauran mutane dake da wannan dattakon da kamalar ba har haka. Mutum daya ta sani haka....SULTANE dinsu. (08187255862 luu luu paying) ★Cikin nutsuwar nan tasa wadda ta zame masa tambari yake takawa a hankali zuwa saman stairs na gidan. Abdii omari da kuma addisaleem suke biye dashi a baya. Omari ne a bayansa....abdii a bayan omari,sai addisaleem dake biye dasu a baya cikin matuqar girmamawa. A nutse yake duban saman,wanda ke dauke da wani irin qawataccen parlor na zamani. Yalwatacce da aka yiwa wani irin tsarin gini aka kuma zuba masa furniture masu wani irin mahaukacin tsada da daukan hankali. Kai ya jinjina a hankali,komai na gidan yayi masa,tsarinsa da komai nasa. Idan iya qasan gidan ka zauna ba zakayi tsammanin zaka taras da wani qawataccen upstairs da yakai kyau tsari da haduwar wannan ba. Ba zakayi zaton samun aljanna duniya irin wannan a upstairs din ba sam,haka ya tsara.....kuma haka yaso tsarin gidan ya kasance. "Ta wanne bangare kuka ajiye library din gidan?" Yayi tambayar yana zubewa abdii idanunshi. Qaramar dariya omari ya saki yana takawa gami da zubewa cikin lausasan qawatattun sofas din da aka qawata parlorn dashi 'yan asalin qasar china hand crafted da suka qawatu qwarai da gaske. "Ka nuna masa daidai inda ruhinsa zai dinga samun sakeena(nutsuwa?" Yana dan boye dariyarsa. Murmushi abdii yayi shima yana shafa sassalkar sumarsa. "Bayan ka sauka qasa,hannun hagu da qofar shigowa" Abdii ya fada yana kwatanta masa da hannu. Kai haisan ya kada a nutse "Yayi....." Hannunsa ya miqa yana cire jakarsa dake kafadar abdii din. "Komai yayi....zan shiga na huta......ka fadawa musu kowa ya wuce mazauninsa......sai gobe idan Allah ya kaimu zamu zauna gaba daya......." "Amma Ousmane haris na buqatar ganinka obbo". Dakatawa yayi da tafiyar da yakeyi ya waiwayo yana duban abdii,har ga Allah ya gaji tubus,tafiya ce ba 'yar kadan ba tsakani Niamey da agadez. Tsananin yadda tafiye tafiye take cikin wasu abubuwa da yake matuqar so ya sanya baiga nisa ba.....bai kuma gaji ba har sai yanzun daya tabbatar ya kawo inda zai huta. Tafiyar awanni goma sha biyun nan a wajensa wani sabon aji ne kuma mabudin ilimi. "Kace ya bani zuwa goben injini" Ya furta a nutse tamkar ba wani gajiya a tare dashi yana kallon yadda abdii din yadan diririce. Zare kallonsa yayi daga kan abdii din.....wani lokaci can baya yana gaza gamsuwa da maganganunsu amjad a kansa. "Idanunka nada wani irin kaifi da nauyi......basan wacce budurwa ce nan gaba zata iya dauke nauyinsu ba har ta tsaya ta fuskanceka da soyayya ko a mu'amala ba......don Allah ka rage magana da idanunka da kake yawan yi........daukemin idanunka haisam......bazan juresu ba". Kadan kenan daga muryoyi da kuma maganganun mutallab game da idanunsa,bai kuma fahinta ba,hakanan bai qara gasgata maganarsu ba sai da qara shekaru saman wadanda yake dasu,shekarun da suka fara fusgar hankulan 'yammata cikin rayuwarsa. "Am.....obbo" Abdii ya sake kiransa sanda ya sanya hannu zai murda handle din qawatacciyar qofar dakin. "Kuma?" Ya fada yana juyawa kadan amma bai kalli abdii ba. "Afwan obbo......saqo ne aka bani......kuma tamkar amana ce da bai kamata ce ban idar da amanarta ba" Shuru parlor din yayi,don tuni omari ya wuce nashi dakin,addisaleem kuma ya sauka yana komawa don tabbatar da shigowar kayansu ciki. Ta baya ya miqawa abdii hannu,cikin farinciki ya matsa ya dora masa a saman hannunsa ya juya da sauri sauri ya lalubi hanyar fita,tun kafin yakai ga duba sunan me saqon,saidai cikin sa'a gajiyar dake taba jikinsa ta hanashi dubawa ya wuce dakinsa da ita a ransa yana raya qila wani sabon shirmene na abdii din kawai. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 37 _________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ____________________________ "Rabbi anzilni munzalan mubarakan wa'anta khairul munzileen" Ya furta da nutsuwar nan tasa dake qara masa kwarjini,take kuma qarawa kyansa kyau,sannna ya taka a hankali ya ajiye jakar tasa saman wani zagayayyar sofa ta hutawa dake wani corner daban na dakin. Da idanu shima dakin ya gama observing dinsa. Da gaske abdii yasan komai a kansa.....da gaske abdii yasan abinda yakeso da wanda bayaso,yasan abinda yake burgeshi dama wanda baya cikin tsarinsa,sai kawai ya furta. "Bismillahillazi la'ilaha illa huu" Ya soma zare kayan jikinsa,don a yanzun wanka kawai yake buqata ko zai warware gajiyar jikinsa. (Ba'a cire kaya haka kai tsaye,saboda idanun shaidanun da suke a muhallinmu,idan kikayi wannan addu'ar Allah xai sanya hijabi a tsakaninku ba zasu ga tsiraicinki ba). Sanda ya fito ya shirya tsaf cikin farar short sleeve shirt fara qal,ya sanya joggers pant shima daya kasance fari. Shigar kaya farare da shigar kaya green wani dabi'a ce tasa da kusan duk wanda ya sanshi ya sanshi da ita. Wayoyinsa ya debo don sanya charge a parlor,yana fita akayi knocking. Daya tambaya sai yaji muryar addisaleem. "Nine obbo" "Shigo" Ya bashi dama kai tsaye yana zama saman wata ottoman dake kusa da socket. Rusunawa yayi kadan sannan yace. "An kammala abinci......bansan ko kana buqata ba". Manyan zagayayyun idanunsa ya daga ya kalli agogon bangon dake manne,dare ya soma yi,ba kasafai kuma yake cin abinci me nauyi ya kwanta ba,don haka ya girgiza masa kai. "Coffee kawai.....gahwa,kar kasa sugar,narkakken ruwan rake ya isa" Ya fada da wani irin yanayi dake dake bayyana qasaitarsa da tabi jikinsa. Kai addisaleem ya gyada sannna ya juya yana ficewa. Kadan kadan sautin karatun hadisai da ake karantawa daga channel din saudi sunnah daga littafin sahihul bukhari ke fita daga tafkekiyar TV din dake zaune dafa'an cikin parlor din,yayin da hannunsa ke dauke da daddadan coffee din,yana kurba yana ratsawa har cikin zuciyarsa. Ya yadda shan coffee da gahwa wani rubutaccen abune cikin jikin oromia......uwa uba ma kuma cikin jinin sarauta,nanaya yakeson kira,muryarta yakeson ji,amma koda ya kalli agogo yanzun goma na dare ne cikin agadez,a jimma kuma yasan sha biyu na dare ne. Idan ya kirata zai tada ne kawai,zai kuma lalata mata tsarin baccinta,don tana kwanciya ne akan lokaci don ta samu ta riski sallar darenta ta kuma sukwane har asuba. Dole ya haqura da kiran nata ya tattara ya wuce bedroom din nasa. A daddade yayi shafa'i da wuturi,wanda komai tsanani baya taba bari su wuceshi,ya cire kayan jikinsa ya saka pajamas,ya tsaya gaban mirror yana feshe jikinsa da night scents dinsa masu lallausan qamshi. Yana tsaka da feshe kyakkyawar qasumbarsa idanunsa ya sauka akan envelope din. Har ya janyesu ya ajiye kwalban turaren ya juya,sai kuma ya dawo a hankali ya dauki envelope din ya budeta ya zaro farar takardar ciki. Rose flower ne qwara daya ta biyo bayan takardar ta fado,ya bita da kallo ba tare daya tsugunna ya dauka ba,sai ya dawo da dubansa kan takardar ya farketa a nutse, Kwantaccen rubutune cikin yaren oromo,ya soma bin rubutun da idanu yana karantawa. _Sallama me cike da aminci da kuma fatan alkhairi,godiya a bisa amsa gayyatar abba na zuwa cin abincin dare tun a wancan lokacin,a wannan karon ni da kaina nake roqon wannan alfarmar don sada zumunci da kuma samun lada.......Menelik ce_ Sai number wayarta har guda biyu a rubuce daga qarshen takardar. Kansa ya daga a nuts,ya cukuikuye takardar yayi cilli da ita a inda baisan inane ba,ya daga qafarsa yana qarasawa bakin gadon. Hannu ya saka ya zuge net din dake kewaye da gadon,sannan a hankali ya shige ciki yana yaba tsarin da aka yiwa gadon kansa. "Allahumma innaka kalaqta nafsi,wa'anta tawaffaha,laka mamataha wa mahyaha,in ahyaytaha fahfazha,wa in amattaha fagfir laha,allahumma inni as'alukal afwa wal'afiyah" Lafuzzansa kuma addu'arsa ta qarshe kenan a kowanne dare idan ya kwanta,yau dinma da ita ya rufe,ya lullube idanunsa yana fatan kasancewa cikin wadanda Allah zaiwa alfarmar ganin washegari. ★★★★Sau uku tana duba tickets ko zata samu jirgin da zai tashi daga Niamey zuwa agadez koda ranar laraba ne amma sam sam babu. Wani abu daya sake quntata ta,ya kuma sake sanya ranta yayi matuqar baci. Kamar yau dai,duk data kasance litinin ce,tana cikin ranakun da takan jima a company ba tare data dawo gida ba,amma litinin din yau din ta zama ta daban. Don tun break din da ake fita da azahar ta umarci driver dinta ya maidata gida. A kebantaccen balcony dinta ta zauna bayan ta canza kayanta,tayi zaton zata iya sake rage wasu ayyukan a system dinta amma saita kasa,ta koma laluben ticket din da zai dace da ranakunta amma ta rasa. Tsaye kawai tayi goye da hannayenta jikin qarfen balcony din,iskar dake kadawa daga hagu zuwa dama suna wasa da gashin kanta da muddin tana gida basu fiya shiri da dan kwali ba. Dogon wando ne a jikinta sakakke,sai shirt me gajeran hannu rounded neck data fidda qirar qirjinta da kuma shafe din shafaffen cikinta da ya bawa mazaunata suma damar fidda nasu shape din. Banda lemo ba abinda yake dirkawa cikinta,duk wani hanya da zata samu gutsiren dalilin da ya sanya sultane mata irin wannan kiran gaggawar ta kasa samun kowanne labari,koda daga gurin mammina kuwa,don hatta mammina dinma bata da labarin kiran saida akhnan din da kanta ta gaya mata. Bacin ran taji yana neman mata yawa,don haka ta miqa hannunta ta dauki headphone dinta dake maqale ta dora saman kanta,ta kuma lalubo waqar best artists dinta cikin mawaqan dake waqa da French wato indila..... Waqar love story ta kunna,ta qara volume din daidai yadda zai ratsata,ta maida idanunta ta lumshe. Tanason waqar sosai,batasan kuma iya adadin sau nawa ta taba saurarenta ba,har wasu baitukan sun zauna a kanta. Amma kuma duk da haka sau daya tak ta taba kallon video din waqar.......tana against duk abinda ke cikin waqar idan ka cire waqar kawai,sautin yana mata dadi sosai,ya kuma bata nutsuwa a ranta.....amma sam video din bai mata ba. Bataga wani dalili bane......bataga kuma wacce irin qaddara ce zata sakata dakon son wanda ya mutu ba.......ko rayayyen ma bata fata qaddararta ta zana mata haka. Bata hangi komai ba cikin so sai qasqantar da mutum......ta sanya duk qarfi da izzarka kayi qasa,itakam duk wani abu da zai sanya kima da martabarta da kuma izza da ikonta su tabu to babu ita a cikinsa. Yadda ta saka volume din ya sanya sam bataji sallamar da barratu ke yi ba,har zuwa sanda waqar ta qare,ta zare headphone din a kunnenta. Haka kawai taji yana sha'awar maimaita kallon film din the umbrella of Cherbourg. Batayi zaton ganin barratu a gurin ba,wannan ya tsoratata sosai. "Afuwa ranki ya dade.....inata sallama amma baki jini ba" Sosai ta shaqi iska ta kuma fesar,ta lumshe idanunta ta budesu sosai a kanta. "Shine me?.....shine zaki tsayamin a guri?.....da izinin wa?" Qasa ta sakeyi da kanta,don ta fahimci cikin kwanakin izzar tata ce ta motsa "Tuba nake" Ta fada a sanyaye. "Karki kuskura ki sakemin wannan haukan.....bacemin da gani kafin raina ya qarasa baci". Da hanzari barratu ta juya tana barin gurin. Ba wani baqon abu bane a wajensu,dama kura ce tayi lafiya ai......lafiyar tata kuma sanadin dauki ba dadin da suka dinga yo ne da morsa safiyya. A duk sanda zatayi musu wani abu na rashin martabawa ko girmamawa......muddin ya fada idanu ko kunnuwan morsa safiyyan saita dakatar da akhnan din.....tun abun yana mata zafi,tana ganin yarfata take,wulaqantata take gaban bayinta kuma hadimanta,har ta fahimci morsa safiyyan ba zata fasa mata gyara ba ko a gaban waye,dole wasu abubuwan da yawa suka ragu. Ta gama saita system din tayi playing film din kiran mammina ya shigo. Iska sosai taja,ta yiwa birra dake tsugunne tana zuba mata lemon inibi sign na ta bata wayar,ta dakatar da zuba lemon ta dauki wayar ta miqa mata da dukka hannuwanta biyu. Sai data janye qafafunta ta maida saman kujera sannan ta daga kiran tana rungume pillow a qirjinta. (08187255862 luu luu paying) "Hi..." Ta furta da siririyar muryartannan maras hayaniya ko kadan. "Sai yaushe zaki girma ne akhnan?" Mammina tayi maganar tana gyara zamanta hadi da miqa hannu ta karbi yankakken apple daga hannun yalwa dake durqushe a gabanta. "Mammina......indai ina dake......indai kina tare dani bazan taba girma ba" Ta fada a narke tana jin kamar ta koma cikin mammina din ta sake haifarta a matsayin d'iyar cikinta ta halali. Tabbas inda haka zata iya kasancewa lallai ba shakka da tafi kowa sa'ar samun uwa.....irin uwar da zata lullubeka da soyayyar da ba zata baka daman kokawa ba ko kadan. "Gaskiya ne biftu na.......ina fatan kina lafiya ko?,baki sanya wannan damuwar a ranki ba?". Sosai ta sake narkewa cikin pillow din kamar wata 'yar mage.....muryarta a karye tace. " Dole na damu mammina......banason na bata da sultane......banaso nayi masa abinda ranshi bayaso". Shuru kadan mammina tayi tana jujjuya dukka maganganunta a ranta. Akwai abubuwan da ya kamata tayi magana da akhnan akai......amma ba zatace mata komai ba,zata jira har zuwa lokacin da ta yanke gaya mata. "Bana jin akwai wani abu da zakiwa sultane da zaiyi muni har irin yadda kike zato ko zargi ba biftu.....na jima banga soyayya tsakanin uba da 'yarsa ba irin taku.....soyayyarki da sultane daban take a zuciyarsa" Sosai maganganun mammina suka bata wani irin relief data gaza samu tunda sukayi magana da sultane. Ta sauke ajiyar zuciya me nauyi,yana daya daga cikin abubuwan da suka sanya take matuqar son mammina din,take kuma ji da ita a rayuwarta sama da kowa da ya rabeta ko ya jibanceta. Tana bata relief qwarin gwiwa da kuma tabbaci akan duk wani abu da zai tunkareta. Tana nuna dukkanin damuwarta da kulawarta akan kome da zai shafeta...... Wannan shine cikakken banbanci da tazara me nisan gaske data yiwa morsa safiyya.......kuma irin wannan tazarar ko mafiyiyarta ta yiwa morsa safiyyan a cikin rayuwarta. "Me yake faruwa a sahel couture?" Mammina tayi furucin cikin tausa murya. Kiran sahel couture din da tayi ya sanya akhnan bude zara zaran idanunta gaba daya da suka rusuna a dazu. "A sahel.......bazan iya tunawa ba mammina". Wani ajiyar zuciya me nauyi mammina ta sauke da tazarar sakanni sannan tayi magana. " Tabbacin ba cikin nutsuwarki kike ba biftu......shin kin manta muhimmancin da kamfanin yake dashi a tare dake?.....me yasa zaki bari damuwa ta shiga cikin muhimmam al'amuranki?". Numfashi ta jawo tana gyara zamanta sosai cikin sofa din. Da jiya da shekaran jiya dama yau duka dai sunan ta shiga company dinne kawai......amma ba wani aiki da tayi daya shafeshi,ba kuma wanda ta bawa daman ganinta idan ka dauke aisa da Shehinaz,suma kuma bata bari sun mata maganar komai ba. "Mammina.......Je ne suis pas dans le ton(bana cikin yanayin)" Tayi maganar kamar qanqanuwar yarinyar data rasa mafita. Wani murmushi ne ya subuce mata,wanda daga ita sai zuciyarta ne kawai sukasan da fitarsa.....koda yalwa dake zaune gabanta ba zatace ta ganshi ba bare akhnan da bata tare dasu. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 38 _________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ____________________________ "Har yanzu baki gama fuskantar matsayinki ba akhnan.......kinsan girman matsayinki da martabarki a qasar agadez?.......ina kikai jarumtarki?.....me yasa zaki bar qaramar damuwa ta mamayeki har haka?.....ba haka na sanki ba.....ba kuma haka nakeso naci gaba da ganinki ba" Ta furta cikin kambamata da kuma motsa mata matsayinta. Idanunta ta lumshe ta kuma budesu a sarauce. "Ina nan yadda nake mammina.....ban canza ba,bana jin kuma zan canza din.....saidai sultane daban yake a raina....dole damuwarsa dama komai nasa ya zama daban a raina......koda sahel couture a bayanshi take.......da girman qarfinki na amince kiyi abinda ya kamata na dan lokaci kafin komai ya daidaita". Shuru sukayi dukkaninsu,wani abu yana bugawa a tsakiyar qirji da zuciyar mammina.......ta tsuke idanunta daga inda take zaune,tunaninta kuma yana harbawa da nisa fiye da nisan dake tsakaninta da akhnan. "Indai kina da uwa irina har abada ba zakiyi kuka ba.......ki dauki lokacinki.....kiyi amfani dashi har iya yadda kikeso.....mammina dinki zata kula miki da komai.....zata kuma ji miki da komai". " Na gode" Ta furta da wata lanqwasashiyar murya,kuma bata qara cewa mammina din komai ba ta yanke kiran,ta ajiye wayar a gefanta ta zame tana kwanciya. Da sauri yalwa ta miqa hannu ta karbi wayar daga hannunta tana duban yanayin fuskar uwar dakin nata. A nutse ta maida dubanta kan yalwa. "A jikina ina jin akwai wani baqon abu......akwai wani abu na daban ba irin abu ba yau da kullum ba.......bansan me yake faruwa tsakanin sultane da akhnan ba......banga alamun komai tattare dashi ba,kamar yadda baiyi niyyar gayamin ba.....daren jiya mun kasance tsahon daren tare dashi muna hira......amma baicemin komai ba a kanta,bana buqatar tambayarsa komai,kaman yadda baiyi niyyar na sani ba......amma ina buqatar sanin komai din.....yalwa" Ta sake kiranta a karo na biyu. "Allah ya taimakeki" Ta furta cikin girmamawa. "Inason nasan meye wannan?......wanne laifi ne akhnan ke zaton ta yiwa sultane daya hanata nutsuwa......inason insan dalilin kiranta da sultane yayi zuwa agadez a satin nan". Kai yalwa ta jinjina sosai. "An gama ranki ya dade......komai zai kasance a gabanki a bude". Yalwa ta furta cikin bata tabbaci,kamar yadda take da tabbacin a kanta. "Sahel couture.......ina ganin kamar ya kamata a lura da kamfanin nan......sannan ayi amfani da dukka wata dama data samu a wannan taqin......wannan tsukin da kuma wannan lokacin.....lokaci ne me kyau daya dace a kula da sahel couture!" Ta qarashe da fadin sunan da wani harshe wani sauti daya tabbatarwa yalwa dukkana abinda ta fada tana nufin hakanne,abinda ya sanya yalwa komawa ta zauna sosai,tana bawa mammina hankalinta dama awannin rayuwarta gaba daya. ★★★★Ni'imtaccen qamshi ne me wani irin sanyi da laushi kawai ke fita daga ilahirin parlor din dama gidan gaba daya a safiyar ranar,daidai da qarfe sha daya na safe agogon qasar garin agadez dama niger gaba daya. Su biyu ne rak zaune saman qawataccen dining din nasa da aka qawata da kalolin abincin da dan adam ka buqata kowacce safiya,wanda kusan komai da yake kai irin zabin abincinsa ne. Ba wani abinci da aka dafa me yawa,kowanne dan kadanne da bazai zama asara ba koda bai cinye gaba daya. Wata sky blue din kurta ce a jikinsa me daukan idanu sosai,wadda aka yiwa adon zare a wuyanta da hannun rigar da wani kalar zare blue black. Iyakar tsahon rigar gwiwa sai wandonta da a wuyan qafan wandon shima aka yiwa ado da blue black din zaren. Fuskarsa tayi wani fresh kaman yadda hasken qwayar idanunsa tayi wani irin tarwai. Sumarsa dake a kwance luf da wadda ke habarsa da kumatunsa sun sake fidda kwarjininsa sosai da kuma sigar kyansa. Sosai yakejin zuciyarsa fresh......kaman yadda yanayin garin a safiyar farko da ya wayeta a qasar tayi masa,don wata iska me damshi damshi ke kadawa wadda ta sake tabbatarwa da kowanne me rai damina tana tafe,daminar da zata jiqa rayuka da tsirrai da sauran halittu da ni'imomi daga ubangijinsa. Coffee ne a gabansa da aka zuba cikin wani qwataccen cup dake dauke da dan qaramin tray dinsa a qasa. Ba wai coffee din yake sha ko yake kallo ba,dukkan hankalinsa ya tattarasu ne akan malam Ousmane,yayin daya sanya coffee din a tsakiyar hannunwansa,ya zagayeshi yana soke yatsunsa a cikin na juna. Bayanan malam Ousmane haris yake saurara,lokaci lokaci yana lumshe kyawawan idanunsa dake da brown din qwayar idanu wadda bata cika duhu ba sosai. "Finally an samu hanyar shiga sultane palace......kuma wannan itace hanya guda daya da zaka zama ahalin masarautar,don muddin ka zama malami ga d'iyar sultane,suna mu'amalantarka ne tamkar d'ansu......musamman morsa safiyya.......tana da karrama dan adam sosai" Malam Ousmane ya qarasa fada cikin bawa haisan tabbaci. Wata sassanyar ajiyar zuciya ya saki kana ya lumshe idanunsa ya kuma budesu duka lokaci guda akan Ousmane din. "Akwai wani option dinne bayan wannan?" Ya furta a nutse,labbansa masu daukan hankali suna motsawa a hankali. Dan kadan malam Ousmane ya zuba masa idanu sannan ya girgiza kai yana cewa. "A'ah" Can qasan ransa ya gama fahimtar abinda haisam ke nufi. Shigarsa gidan a mazaunin malami ne sam tsarin bai masa ba......to amma kuma ba wata hanyar da tafi haka sauqi. "Kana da wata hanyar da tafi wannan ne sauqi?" Ousmane ya tambayi haisam din yana qoqarin tsareshi da ido. Kai kawai haisam ya girgiza ba tare daya dubi Ousmane din ba,yaja cup din coffee dinsa a nutse yana kurba gami da zubawa wani canister dake gabansa ido. Kurba kusan biyar yayi,shuru yana sake ratsa wajen,Ousmane yayi qarfin halin ajiye ajiyar zuciya. Akwai buqatar ya fahimtar da haisam din,don wanann din wata dama ce babba a gurinsu,wucewarta kuma zai zaman kamar rasa gwaggwabar dama ne. "Shiga agadez palace yana da muhimmancin haisam ka fahim......" "......na fahimta Ousmane......." Ya katseshi yana mai bashi amsa. Can qasan zuciyarsa wani kishin tashi masarautar tana kamashi. Ba inda zaije a duniya sarautar jimma ta sauka daga jikinsa ko kuma zuciyarsa,wata sarauta ce da aka haifeta a asalin cikin jininsa,ta yaya zai iya rayuwa qarqashin wata sarautar?,qarqashin wani tsare tsaren da ba na mooti abba jifar ba?. "Shiga gidan yana nufin sanin mutane da yawa dake rayuwa cikin gidan......mutanen dake rayuwa qarqashin kariya da alfarmar masarautar.......shiga gidan zai zama hanya mafi sauqi ta sanin mutane da dama da cudanya dasu........haka abun yake ba kuma laifi......amma zama malamin d'iyarsa da jikokinsa fa?.......banajin abune me yuwuwa". Haisam din ya fadi yana jin har cikin zuciyarsa abun be gamsheshi ba. "Haka zaka shiga muhammad.......ka sanya a ranka daga yau kaine malami na gaba da zaici gaba da koyar da diyoyinsa........chapter closed,komai ya kammala.......fara gudanar aiki kawai muke jira,don duk wani jan qafa da zai biyo baya,tamkar qarin kwanakin da zakayine cikin aikin" Ya tsinci muryar bobbo muhammad dawud da baisan daga ina take ba. Sai daya daga qwayar idanunsa a nutse sannan ya lura video call ne Ousmane ya daga a wayarsa,fuskar abba muhammad dawud din kuwa ta fito tarwai a wayar,furfurar nan tasa dake nuna shekarunsa da kamalarsa dukka sun fita sosai. Idanu suka hada da haisam din,sai ya jinjinawa haisam kai,ya kuma dunqule hannayensa dukka biyun cikin na juna yana jijjigawa. A hankali shima haisam din ya hada hannunsa hakan,wannan din wani salon alwashi ne da suke ciwa juna muddin zasu fara aiki me wahala da hatsari irin hakan,wani alqawari ne na cika aiki da suke yiwa junansu. Daukewar kiran dif ya sanya haisam maida kallonsa kan Ousmane,suna hada ido ya saukar da nasa idon qasa yana fadin. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Afuwa......bansan shine ya kira ba,bansan kuma na daga kiran kai tsaye ba,duk da already tun jiya mun gama maganar dashi,ya kuma tabbatar ba wata hanyar data wuce wannan......ko ina ya kamata bincikenmu yakai......muna da hadin kan hukumar tsaro har uku dake riqe da qasar nan" Kai haisam ya jinjina kawai baice komai ba,ya jawo wani kyakkyawan mazubi da ake zube dabino a ciki masu laushi da zaqi ya soma barewa,don dasu yakeson yasha tea din. Yana da zabi da madadi ashan sugar,mazarqwaila ko zuma ko dabino,sune abokan zaqinsa. "Akwai yiwuwar sanar da shugaban qasarsu" Haisam ya fada kansa tsaye ba tare daya dubi Ousmane ba daya soma yin hanyar fita. Cak ya tsaya sannan ya dawo da baya da sauri. "Amma akwai hatsari fa ayin hakan......" Dogayen yatsunsa ya daga masa alamun dakatarwa. "Wannan kasadar tawa ce ba taku bace....idan ka fita ka turomin addisaleem". Wani yawu me tauri Ousmane ya hadiye. Yasan halin haisam din,kaifi daya ne......idan yace zaiyi ba abinda yake saukar dashi daga wannan bigiren. Ba lamari bane daya shafi addini ballantana ya jawo masa aya ko hadisin da sune kadai makaman dake iya saukeshi dama.......dabara ce da kuma fahimtarwa,ya kuma fuskanci bashi da buqatar wannan,sai kawai ya juya ya sauka yana kiran mass addisaleem kamar yadda ya buqata. "Dukkan wadanda muka taho dasu daga addis ababa nakeso ka sanar musu,ina buqatar ganinsu nan da awa daya......ka saka abdii a ciki" Ya bawa addisaleem umarni kai tsaye. "An gama" Ya fada yana rusunawa sannan ya juya yana fita a gaggauce. Yana da kiyaye lokaci,yana kuma mutuntashi da martabashi qwarai. Idan shi yayi zabin lokaci don gudanar da wani abun,baya wuce adadin mintuna da awannin daya ware,idan shi aka bawa lokacin,zaiyi komai kaman yadda lokacin yace......idan abune kuma ya saka awa nawa zai dauka......baya shallake wadannan awannin yake qoqarin kammala komai. Cikin kamala ya sauko zuwa dakin da ya gama wareshi a mazanin dakin da zai kasance wajen ganawarsa ta sirri da dukka wanda yakeso. Kaman yanzu dai da mutum shida harda abdii na bakwai suke jiransa. Sosai yayi wani irin kyau da kwarjini cikin shigar wani kyakkyawan yadi da aka yiwa budadden dinki kamar rigar fulanin Nigeria,saidai ita din tafi tasu fadi sosai ta kuma sauka har gwiwarsa. Farar riga tas yayi amfani da ita daga cikin rigar saman,sai dogon wando shima da yake mahadin kayan a jikinsa. Kyakkyawan nadi ne a kansa da yayi kamanceceniya dana buzaye,saidai akwai banbancin salon nadin da kuma yanayin yadin da baikai na buzaye kauri ba,saidai ya lullube ainihin kyakkyawan fuskar nan,sai zagayyayun manyan idanunsa da hancinsa me tudu daya bayyana ta cikinsu. Da cikakkiyar sallama ya shigo gurin,sallamar data maida kowa cikin hankalinsa suna hada baki wajen amsawa,sannan suka tattara masa hankalinsu. "Ku zauna" Ya fada yana nuna musu kujerun da hannunsa. Sai da kowannensu ya zauna sannan shima ya janye pillow din dake saman kujerar da tafi kusa dashi ya zauna. Wani irin zama daya sanya dukkaninsu kallonshi,kusan ya saba da zaman ba kuma don yana nufin izza ko iko ba,aah.....kawai ya zame mishi jiki kusan a dukkan wani yanayi da zaiyi magana me matuqar muhimmanci,a gida ne ko a office. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 39 _________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ___________________________ Salawi beeno da hambal suna cikin hadimansa mafi kusaci da mooti yace dole su kasance a tare dashi cikin tafiyar. Yace sam bai yarda ba,bazai kuma bari ya tafi gayarshi wata qasa da sunan aiki ba ba kowa a tare dashi. Duk da tsarin aikinsa,wani sirrintaccen aiki da ba kowa yasan yana yinsa ba.......da yawa suna masa kallon fitaccen kuma gawurtaccen yariman dake kawo duk wani nau'ikan turaruka masu tsananin tsada daga india da kuma daular larabawa wato dubai. A zahiri shine kasuwancinsa,wanda yayi matuqar karbarsa da wata irin nasara da bai taba kawota a kanshi ba. Ya zabi maida hankali a kanta ne saboda tsananin soyayyarsa da qamshi da kuma turare,abu na biyu kuma ya dauke hankulan mutane daga laluben meye aikinsa da sana'arsa?,sai gashi harkar ta maidashi wani boyayyen attajiri da da yawa mutane basusan waye mamallakin manyan kamfanunuwan turare 3stars guda uku daya mamaye Ethiopia da dukka qasashen africa ba.......hakanan basusan waye ainihin mamallakin gonakin nan masu Tsananin girman dake gigita manoma ba,wadanda suke noma ganyan turarukan da ake zuwa a siya a fiddasu qasashen qetare ba. Takai ta kawo ganyayyakin nau'ikan turaruka da yawa ana nomasu cikin manya manyan gonakinsa guda goma sha biyar da yake dasu,saidai ya saida a kuma sarrafa masa zuwa turare da nau'in qamshin da kamfaninsa na 3star kawai ke da irin wannan qamshin. Ba huruminsu bane susan abinda ya kawoshi agadez,amma yasan dole akwai sharuddan da zai gindaya musu su kiyaye karsu bata masa aiki,don haka bai soma dasu hamdii ba juniors dinsa a hukumar,sai ya fara dasu salawi. "Ba kowacce tafiya bace take buqatar dogon bayani sharhi ko fashin baqi ba......munzo agadez kamar yadda kuke gani. Baquwar duniya ce a wajenmu,duniyar da ba tamu ba. Baqin mutane da kuma baqin al'adun daya zama dole kowa a cikinku yasan ya suke?,ya kuma zaiyi mu'amala dasu". Zamansa ya gyara yana soke yatsunsa cikin na juna. "Kamar yadda nake yawan fada muku a jimma kuka kasa aiki da abinda nake fadi din,a yanzu ya zama tilas kuma wajib kuyi aiki da wannan......don nan din ba jimma bane......kuma a nan duk wani sabawa doka tawa hukunci zai iya hawa kan kowa a cikinku" Motsawa kowannensu yayi cikin mamakin furucin daya fada din. Mutum ne me tsananin uzuri,kauda kai da kuma sassauci sau da dama. Ba zasu iya tuna yaushe yayi hukunci a karan kanshi ba akan abinda ya zamana an masa laifi ne,ba abinda ya kasance cikin haqqin Allah da manzonsa ba. Kai ya jinjina musu a nutse,alamun yana nufin abinda ya fada din. "Ordinary mutum nake kaman kuwa koda a jimma ne......inason kusa a ranku a yanzun da muke agadez. Zan iya ganinku na wuceku kamar ban sanku ba,kamar yadda kuma zaku wuce ni kamar baku sanni ba idan ba ni na buqace ku ba. Ba batun obbo......ba batun prinsii.......a agadez sheik haisam zallah nake......idan kunso ma kuce haisam sak". Duban junansu sukayi su dukka shidan,bawai iya su salawi kadai ba,hatta dasu hamdii maganar ya musu nauyi. Sosai ya tsaresu da kaifafan idanun nan nasa,yana sake tabbatar musu da abinda ya fada din haka yake nufi. "Zakuyi rayuwarku da duk kalar 'yancin da kukeso.......saidai bazan lamunci sabawa dokar Allah ba,a duk sanda nake buqatar ku zan sanar daku hakan" Shuru sukayi dukkaninsu suna juya maganganunsa. Wacce irin rayuwa zasuyi haka cikin agadez din?,ta yaya zasu iya kiran sunansa haka gatsal?,ta yaya zasu rayu dashi a gurabe daban daban ba tare da bashi kariya ba kaman yadda mooti ya buqata?,ya zasu iya banzatar da wofantar da amanar mooti?,ya zasu iya yin nesa da baya baya da prinsii din nasu.....wanda ya kasance abu mafi soyuwa a zukatansu?,abu me girman daraja sosai a idanunsu dama qasarsu?. "Kowacce kalmata guda daya tana da gurbi da muhalli.....kowacce kalmata guda daya rubutacciya ce kuma me amfani.....ya kamata ku kiyayesu da kyau,idan akwai buqatar wani abun kuma kuna iya sanar da abdii.....zaku iya tafiya" Ya furta yana nuna musu hanya. Jikinsu a sanyaye suka miqe suna nufar qofa har suka kammala ficewa. "Don Allah obbo kada ka kafamin kalar sharadin daka kafa musu.......na rantse bazan iya kiyayewa ba" Abdii ya soma fada tun kafin haisam yakai ga cewa komai. Wani lallausan murmushi da haisam bai shirya yinsa bane ya subuce masa. Yayi qasa da kansa yana dan jan hancinsa kadan kafin ya daga kansa yana duban abdii da kyawawan idanunsa. "Da gaske karaya nake gani cikin idanunka abdii" Ya fada yana dage cikakkun girarsa dukka biyun. Narai narai abdii yayi yana dubansa. "Ai nace maka bazan iya ba obbo.....don Allah karka sakani cikin sharuddansu" Kai kawai ya girgiza sannan ya maida dubansa kansu hamdii. "A cikin gidannan ko a masaukinku ne kawai na sanku a yayin da muka kebe......amma a waje baku sanni ba ban sanku ba....." "Baku sanshi ba bai sanku ba" Abdii ya furta yana gyara maganar gudun kada ayi jam'i dashi. Idanunsa haisam ya watsa masa,saidai still har yanzu yana ganin wannan tsoron tattare da abdii. "Will you keep quite?" Ya fada a nutse,sai abdii ya kama bakinsa,ya kuma koma gefe yana jin yadda haisam ke tsara komai tsakaninsa dasu hamdii cikin salo da cikakkiyar qwarewar aiki har suka kammala. "Kowa ya zaman kusa da na'urarsa,a kowanne lokaci xan iya buqatar wani abu daga gurin dayanku.....ku sauka lafiya" Ya sallamesu sukayi saluting nasa suka fice. Shuru dakin ya dauka,sai haisam din ya miqe a nutse yana takawa da nutsuwar nan tasa. "Inason naga yadda garin yake.......inason insan wani abu ko ba yawa game da gidan sarautar agadez" Wani farinciki ya kama abdii,ya miqe da sauri yana jin dadi yana ratsashi. Koda haisam bai fadi a fili cewa zai zamana na hannun damansa ba,bawai boyayyen amini ko majibancin lamarinsa ba......yadda ya zabeshi a yanzun a matsayin wanda zai rakashi zuwa cikin gari kadai ya bashi amsarsa. Kallon haisam kawai yakeyi,yadda yayi shiga ta cikakkun buzaye,tun daga tufafi zuwa rawanin kansa. Satar kallonshi kawai yakeyi,har sai da haisam ya gaji da kallon ya damqi wuyansa sanda suka miqe sosai kan titinsu. "Wannan kallon is too much fa,ba mace bane kai,namiji ne" Cikin boye dariyarsa abdii yace. "Bansan yaushe kasan al'adar mutanen nan ba,har ka iya nadinsu da shigarsu obbo......" Kai ya girgiza "Ina mamakin yadda kuke daukan aikinku bada muhimmanci ba......a lokacin da kake wata sana'a,ya kamata ka zama qwararre a kanta......ka birkida zuwa dukka launi da kalar da akeso ake kuma buqatar ka zama" Kai abdii ke gyadawa cike da gamsuwa,don sosai ya fahimci abinda haisam din ke nufi. "Kuma shigar tayi maka mugun kyau obbo....." "Kama bakinka abdii" Ya fadi masa yana duban hanya sosai sanda yake hango wasu baqaqen motoci masu tsananin sheqi suna wulwula gudu saman titin. Kyawawan motoci ne guda hudu da dukkaninsu suke kama da juna,saidai guda daya a cikinsu tafi Kowacce kyau da girma da kuma alamun tsada. Sosai haisam ke qoqarin nazartar motocin,har zuwa sanda suka zo suka gilmasu da wani irin gudu. Kadan ya waiwaya yana kallon plate number din dake manne a bayan motar,wanda ya fuskanci dukka iri daya ce. PRINCESS AKHANAN shine abinda ke rubuce a kowacce mota,sai lambobi daga daya zuwa hudu. Kansa ya dauke a hankali,yana duban abdii daya matso da zummar kade masa 'yar qurar da ta hau jikin kayansa. Da idanunnan nasa masu nauyi ya dubi abdii,magana kuma yayi masa da idanu wadda ta sanya abdii din janyewa baya da sauri,sai ya miqa nasa hannun yana kade qurar. "Khadeeja Muhammad hammud" Maheer ya fadi yana duban titin da motocin suka wuce,wanda haisam ya fahimci ba wata mota data biyo bayan tasu har sai bayan da suka wuce din,abinda yake alamta masa kamar wani tsararren abune da dukka masu ababen hawa a garin agadez suka saba dashi lokaci irin wannan. "Zuciyar sultane ce.....diya qwara daya da sultane yake ji da ita,diyar kuma data zama wani abu mafi girman daraja da tsada da sultane yake dashi a duniya" Idanu haisam ya lumshe sannan kuma ya budesu,yana jin maganganun Maher din a wani muhalli da sam bai gane masa ba. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Idan kace ita daya ya mallaka bakayi laifi ba.....duk da a zahiri diyoyinshi guda biyu ne.......sangartacciyar 'yar gatar da ake tattalinta da dukka abinda takeso.......da kuma dukka abinda taga dama takeso ya wanzu a yadda take muradi. Tana hukunci tana alfarma,tana kuma zartarwa dukka a qarqashin nata ikon,saidai wani abun mamakin kuma.......ba wani wanda zai iya baka cikakken siffa da kamanninta,don ganinta ido da ido a gurin jama'ar yankin nan bai zama abu me sauqi ba". Wani abu haisam ya hadiye a hankali yana qoqarin faffasa kalaman Maher,yanason kawo daidaito tsakanin maganganunsa dana Ousmane. "Akwai maganganu da yawa a kanta ga wadanda ke rayuwa kusa dasu.......tana da wata irin izza girman kai da alfaharin daya zarta na mahaifinta.......tana da tsare tsare da dokokin da muddin zaka rayu tare da ita dole ka kiyayesu.......har ila yau......ita daya ce tilon macen da take iqirarin har a yanxu ba'a haifi nau'in namijin da zai dace da rayuwarta ba.......har yanzu babu namiji irin nau'in ajinta....." Idanu abdii ya waro yana duban haisam da gabansa kawai yake kalla,hankulansu suna rarrabuwa kashi kashi. Yanayin unguwar da suke tafiya a cikin ta,yanayin mutanen dake kai kawo jifa jifa,sai wani dan qaramin kaso na hankalin nasa daya miqa akan maganganun Maher. Dukkan alamu sun tabbatarwa abdii hankalin haisam baya kai dari bisa dari,sai ya janye idonsa daga kan haisam din ya mayar kan Maher yana mamakin me ya hana wannan baqon labarin da yasha banban da labaran da suka saba ji da gani su dauki hankalinsa?. "Amma ita din wacce irin halitta ce ita?......yaya take?......wani irin launi gareta da dukka mazan duniya basu tsaya a mataki da cancantar samun aurenta ba?". Sosai shima Maher yake da nutsuwa,irin nutsuwar da zai wahala ka fuskanci shi din daya daga cikin ma'aikatan NISS Ethiopia ne. "Mutum ce kamar kowa......amma nasha jin hirarta a bakunan mutane a guri daban daban da lokuta daban daban.....mutum ce amma tasha banban da tarin Mata........tana da wani kyau kwarjini da kebantattun abubuwa da naji suns cewa ta cancanci zaben duk kalar mijin da takeso.....ko waye ko wanne iri ne......" "Meye alaqar koya karatuna da yaran sarki da ita?" Yayi tambayar ta kai tsaye ba tare daya kalli Maher ba,don yanason banbamce wasu abubuwa da baiso su zama cikin qurataccen lokaci. Uwa uba ya gaji da jin soki burutsun bayanai a kanta......abu guda yakeson tantancewa shine.......ta kasance bata cikin mutanen da zasu fado hanya ko gonarshi. Girman kai......izza da raina mutane,wasu dabi'u ne da yanzu yanzu suke raba tsakaninsa da kai. Wasu dabi'u ne da ya tsana yayi matuqar yin hannun riga dasu. "Tana Niamey tana gudanar da kasuwancinta.......itace CEO na SAHEL COUTURE" A nutse haisam ya maimaita sunan kamfanin can qasan ransa. Kalman CEO babbar muqami ne ko matsayi a kamfani. CEO yana tsaiwa akan komai da komai daya shafi cikin kamfanin dama wajensa......to amma ta yaya tana da wannan matsayin fuskarta ta zama wata boyayyar aba?. "Zanso naga wannan......." Abdii ya soma fadi,saidai baikai ga qarasawa ba haisam din ya tari numfashinsa "Abdii" Ya kirashi still idanunsa yana kan hanya. "Obbo" Ya furta yana maida hankalinsa jikinsa. Daga yanayin haisam Maher ya fuskanci baya buqatar hirar......hirar kuma bata dace da mode dinsa ba,don haka bai sake cewa komai akai ba,har zuwa sanda sukayi doguwar tafiya sosai. "Ina buqatar qarin sani akan komai daya shafi cikin gidan......sauran zan bincika da kaina" Ya fadi yana tattara hankalinsa guri daya. ★★★Cikin girmamawa kowacce qofa ta gidan da masu tsaronta mataki mataki take motsawa tare da budewa don samun damar shigar motocin dake dauke da akhnan din cikin ainihin ginin gidan. Basu tsaya ba har sai da sukakai gurin ajiyar motoci na musamman na cikin gidan,wanda ke dauke da tarin motocin sultane dana mammina da ragowar na akhnan din,harma dana morsa safiyya wanda ba kasafai ta fiya hawansu ba. Tun kafin motocin su kammala tsaiwa take iya hangen mammina din. Tsaye cikin adon nan nata da kowanne lokaci yake qara nuna ita din matar sarki ce.....matar babban mutum me alfarma ta daya sultane muhammad hammud. Iya suturar dake jikinta kawai wani babban jarinne a gurin dubbunnan mutane,daga bayanta kuma hadimanta ne su biyar,ciki harda yalwa ta hannun damanta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 40 ___________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ____________________________ Dauke idonta tayi tana sauke ajiyar zuciya,jikinta duka a mace yake kuma a sanyaye,saboda har yanzu bata da tabbaci ko tartibin abinda zai faru da ita. Alamun bude mata murfin motar ne ya dawo da hankalinta jikinta,ta fidda numfashi me nauyi tana jin yadda zagin gidan yaketa wasata "Gaba salamun baya salamun......barka da isowa zuciyar sultane.....tauraruwar qasar agadez......me alfarma 'yar masu alfarma,wallahi ganinki kadai ya ishi bawa alkhairi,zamanki tare da mutum alfarma ce,qarin daraja a wajensa,sukari me farin alkhairi,bango majinginar bayi........me kyauta da hannun damanta hagunta bata sani ba,me darajar da babu ta biyunta.....ga khadijatul kubra". Sau tari yadda zagin ya iya tsara da jero kalamai a kanta abun yana matuqar burgeta,uwa uba kuma ba wanda yakewa sai ita daya,koda sultane kuwa baya yiwa,ita kadai ya tsayawa yake yiwa,shi yasa sosai take sakar masa kudi. Mutum ce ita me amana,meson kuma mutum me amana. Wannan ya sanya zai wahala kayi magana da ita ma ka jita a gurin koda su aisa ne,amanarta da zallar miskilanci da izzarta ma ba zasu bari ba. Amma a yau din sai takejin kirarin nata yana damunta har cikin kanta. Ta daga ido tana duban wanda ya bude mata motar,mammina ce da kanta,ta miqa mata hannu kuma tana sakin mata murmushi,take taji zuciyarta ta karye,wani qaunar matar yana sake ratsata,qauna tsantsa mara algus a ciki. Rungumeta tayi a jikinta tana fadin. "Sannu da zuwa......sultane ya sakamin ke a gaba gashi ya jawo miki tafiyar mota,Allah ya rabaki da ciwon jiki". Ido kawai ta lumshe,tana jin dadin yadda mammina ke kula da ita,tana jin dadin yadda mammina ta damu da damuwarta,suna raba farinciki da kuma baqinciki tare da mammina din......suna raba samu da asara a tare,suna raba ciwo da lalura dukka idan suka sameta,wasu abubuwa kenan da bata taba hangensu ba ga matar da ake faman kira UWA a gareta. To wai ta yaya ma zata iya raba wannan qaunar?,wannan soyayyar?,da wannan kulawar?. Batasan ta inda zata fara azasu akan mizani guda daya ba sam sam sam. A hankali ta daga kanta daga jikin mammina din tana dubanta. "Kinsan dalilin kiran sultane a gareni?" Ta fada da muryarta me laushinnan wadda ta qara sirancewa. Murmushi mammina ta saki tana kai hannunta fuskar akhnan din. "Na fiki son insan dalilin da yasa ya kirakin tun kafin ki iso" Ta furta wanda har a qasan zuciyarta hakan take nufi,saidai kuma ta lullube da wani bayanin. "Don bana qaunar abinda zai taba farincikin wannan halitta komai qanqantarsa.......koma meye ni nasan bazai taba yin abinda zai cutar dake ba,koda ace fushi yayi........amma koda irin hakan zata iya faruwa,ni ina bayanki,ina kuma tare dake a duk wani hukunci da sultane zaice zai yanke". Wannan tsadadden murmushin nata ta saki,ta dora hannunta saman hannun mammina dake fuskarta,labbanta dake da pink color ya motsa a nutse tana furta kalmar. "Na gode" . Inda akwai wani matsayi a duniya da yafi matsayin mahaifiya,tabbas da zata bawa mammina shi,don ta cancanci hakan. "Ku kai mata su sassanta,zamu wuce ciki da ita" Mammina ta juya cikin isa tana bawa su buhaina umarni,wadanda suke dauke da handbag din akhnan wayoyinta da wata 'yar qaramar jakarta guda daya data saka suka zuba mata abubuwanta masu muhimmanci da zata iya buqatarsu,saita riqe hannun akhnan sosai cikin nata suna wucewa zuwa sassanta tana qoqarin sako mata labaran da zasu dauke hankalinta. Sosai akhnan ta cika da mamakin tarbar da mammina ta shirya mata,tamkar wadda tayi wata tafiya ta shekara da shekaru bata nan. Kalolin abinci da abubuwan sha iri daban daban,gyara na musamman tasa aka yiwa dakinta dake sassan mammina din,wanda a baya cikinsa take rayuwar quruciya harta zama budurwa sanda aka wareta daga sassansu. Ta ajiye mata abubuwa masu yawa da tasan tana sonsu,sai akhnan din ta tsaya kawai tana kallon komai kamar almara,kafin ta mayar da dubanta kan mammina din. Girarta dukka guda biyun ta dage mata alamun yes,sai kawai akhnan din ta fada jikinta tana sakin shagwababben kukanta. "Ya isa mana babyn sultane" Ta fadi da wani salo can baya da ake kiranta dashi. Janyeta tayi saman wata tattausar qaramat Royal chair dake dakin tana qoqarin kwantar mata da hankali,bata bar dakin ba sai data tabbatar ta samu nutsuwa. "Akwai sauran lokaci,ki wanka ki huta kadan,don sultane ya fita,amma a gida yace zaiyi sallar isha'i,kafin sannan saiki shirya ki shiga ki gaida mommanki". Duban mammina tayi,tana jin ranta yana baci yanzun nan. " Momma na?" Rai mammina ta hade tana kuma daga mata kai alamun eh. Yadda yanayin mammina din ya canza ya hanata sake cewa komai,sai ta miqe kawai ta soma zare kayan jikinta. Ta kammala tsaf ta barsu a zube a gurin ta daura towel tana wucewa bathroom din dake da sassa biyu,toilet da bathroom din kansa. ★A nutse sanye kuma da budaddiyar abayar data rufe ilahirin jikinta ta kuma sake qawata shigar tata da dan qaramin Malaysian hijab take qarasowa inda morsa safiyya take. Kebantaccen guri ne da ta ajjiyeshi kawai saboda ibada,ko da tsakiyar dare,ko bayan sallar magariba ko bayan sallar asuba. Daga kai tayi tana duban falaak din sanda take zama a gabanta,takai qarshen addu'ar dake bakinta sannan tace. "Ya akayi?". Kadan tadan yamutsa fuskarta. "Tun dazun akace tazo.....amma banga ta shigo gaidaki ba momma" Sosai morsa safiyya ta zubawa falaak idanu,tsoro yana neman yin tasiri a ranta. Tsoron wani abu takeyi,tana tsoron faruwar wani abu.....wannan abun kuma da idan ya farun zai sake jaddadawa zaitun nasararta. Wannan jarumar zuciyar tata ce ta motsa,ta kuma mamaye duk wata fargaba tata. Murmushi ta saki tana ajiye dan qaramin littafin azkar din dake hannunta. "Annabin rahama S A W yana cewa:- duk wanda yayi imani da Allah da ranar lahira,ya girmama baqonsa.....biftu a yau da kuma kwanakin da zatayi tabar gidan nan duka baquwarmu ce.....ke me kikayi don girmamata a matsayinta na wadda take gaba dake?" Morsa safiyya takai qarshen maganar tana duban idanun falaak. Idanu falaak din ta zubawa momman tata,so take ta bambance kariya momma take bawa akhnan ko kuma dai tana fadin abinda da gaske haka ya kamata ya kasance?. Ta karanci hakan a tattare da ita.......ta kuma gane me takeson karantowa,don haka ta sake lullubeta. "Kin manta?,kinmin alqawarin kusantar da kanki da ita?,kinmin alqawarin zaki tayani ta koma kamar yadda nakeso?,ina wannan alqawarin falaak?". A hankali sai fuskar falaak din ta washe daga wani kaso zuwa qasa da hakan. "Na sani,nice nayi alqawarin,kuma zan cikashi momma" Dubanta morsa safiyya keyi tana jinjina kai. Koda falaak bata daukota a komai ba,amma ta dauko dabi'arta ta cika alqawari......ta dauko halayyarta ta cika magana muddin ta fadi zatayi,don haka ta bita da murmushi. "Naji dadin hakan,Allah yayi miki albarka,ya kuma baki damar cikawa kaman yadda kika dauka". "Ina zuwa" Falaak din ta fadi tana miqewa a nutse da zummar ficewa a dakin,sai hakan ya tunawa da morsa maganan da sukayi da ustaz Ousmane dazu. "Gobe bayan sallar la'asar sabon malaminku zaizo,zaku dinga zama karatu juma'a da asabar,qarfe hudu da rabi na yamma zuwa shida,awa daya da rabi zai dinga yi ba kaman ustaz Ousmane ba da yake awa biyu ba harda rabi......yana da qa'idojinsa,bayaso kuma a karya masa su". Fadin qa'idojin ya sanya falaak dakatawa,ta kuma waiwayo sosai tana duban momma fuskarta na yamutsewa. Fata take kada dokokinsa su zamana masu tsauri kuma masu takura......don muddin hakan ya kasance bata jin tafiyarsu zatayi tsaho. Ta sani,ba wani hukunci da zai musu momma ta qalubalanceshi,duk dama bata tunanin koda kallon banza akwai malamin da zai iyayi musu ballantana kuma takai ga hukuntawa. "Dole ku dinga rigashi isa gurin karatun kafin ya qaraso.....idan ya rigaku isa har sati uku a jere akwai hukunci" Momma ta fadi murmushi yana subuce mata. Haka kawai takejin abun da malamin yana burgeta. Ba abu bane me sauqi don zaka koyar da yaran masarauta......masarautarma diyoyin cikin sultanr ka rattaba musu dokoki hankalinka kwance,bin dokokin kuma shine damarsu ta daukan karatu a wajenka. "Momma......baisan......" "Ya sani,kada ma ki tambayeni,amma hakan shine daidai,kuma a raina naji cewa sai yanxu kuka samu malami irin malamin da nakeso,duk da ban sanshi ido da ido ba.......girmama karatu akan dalibi dashi.....kasan girma da martabar abinda ake koya maka,kin manta ne?". Kai falaak ta jinjina,duk da haka tana jin kamar ya cika jaye jaye da yawa. "Allah ya kaimu" Ta fadi kawai tana juyawa tana fita a dakin,a qasan ranta kuma tana juya wanne irin malami ne wannan?. Duk da takan shiga kitchen lokaci bayan lokaci,don girki yana daya daga cikin abubuwan da sukan bata nishadi,amma sosai a yau ma'aikatan dakin girkin sukayi mamakin shigowarta da kanta. Sun sani,tana da sauqin kai irin wanda sam ba zaka hadashi da na 'yar uwarta ba.....tana da sassauqar mu'amala da kowa ma zata iya mu'amalanta. "A hadamin duk wani abu me muhimmanci da akasan yaa biftu tana son ci yanzun nan......nimra ki zubasu a kwando zamu wuce sassan mammina". Sak kowa yayi cikin kitchen din,har ita da kanta ta karanci haka,saita dakata da zabar inibin da aka shigo dashi yanzu cikin kwando me yawa ta kalli fuskokinsu. "Lafiya dai?" Ta tambaya tana son jin amsa. "Ai ranki ya dade.......ba wanda yasan abincin da tafiso taci kaf gidan nan......inajin illa mutum uku,giwa mammina......buhaina sai birra" Girarta tadan yamutsa abun yana daure mata kai. Wasu abubuwan idan aka fadesu a kanta sai taji tamkar ita ke mulkin bawai sultane ba. Tayi shuru tana nazari kafin ta sake cewa "Koda dan wani abu qanqani da tafiso ba wanda yasan satar amsarsa?" Shuru kitchen din ya sake dauka,kaman ba za'a samu me magana ba kafin nimra tace "Abu daya zuwa biyu na gani......ana yawan kai madara sashenta,sannan ana yawan shiga da kayan itatuwa,duk da ba kowanne nau'i naga ana shiga dashi ba" Kai falaak ke jinjinawa. "A shirya iya wadannan ababen.......a hada da kilishi da zuma,in kin kammala nimra ki sameni a bakin mararraba". "An gama Allah ya taimakeki" Ta amsa cikin girmamawa hadi da rusunawa sannan ta juya tana komawa can cikin kitchen din,ita kuma falaak din ta fice. Da mutum uku suke nufar sassan mammina din. Duk da dare ne amma kowacce qofa kowanne taku cike yake da dakarun dake tsaron sassan. Duk inda tazo giftawa gaisuwa suke kaiwa sannan su bude mata hanya ita dasu nimra su wuce zuwa ciki. Daidai lokacin da akhnan din ke zaune cikin dakin nata,tana saman wata armchair. Ta dora habarta kai hannunta riqe da wayarta tana scrolling a hankali. Wani statistics na company neesha ta aiko mata take dubawa. A zahiri tana kallo ne kawai,amma a badini ba abinda take fahimta,tana dakon jiran kira ne kawai daga sultane,daga ina kiran zaizo?,me kuma zai biyo bayan kiran?. Da sallama a bakin falaak ta tura qofar dakin tana shiga. Bata dago ba akhnan din bata kuma juyo ta dubi me shigowar ba. Kawai tana son gane waye ya keta mata doka ya shigo mata daki haka Kai tsaye a sanda ta buqaci kowa yayi nisa da ita?. "Yaa biftu" Sunan da aka kira din ya kawo mata zaton falaak din ce,saita miqe ta zauna sosai tana kuma waiwayowa ga falaak din. Idanunsu ne suka gauraya dana juna,dukkaninsu kowa abu na daban na sauka qasan ransa. Ta dauka zata rufe falaak da fada ne kaman yadda ta qudirta a ranta sanda ta miqe ta zauna,amma sai taji wannan qudurin yana zagwanyewa sanda falaak din ke qarasowa cikin dakin bayan ta ajiye kwando na biyu data amso daga hannunsu buhaina da iyakacinsu wancan parlor din na farkon farko. Har yanzu da wannan murmushin akan fuskarta,saita tako kanta tsaye ta qaraso gabanta ta zauna tana tura mata kwandon. "Naji kinzo......tun daxun banga motsinki ba,nace bari na shigo mu gaisa na karbi tsarabata kuma" Tayi maganar da irin yanayin daya sanya take akhnan din taji girma ya motsa mata. Irin girman da yaya takeji akan qannenta,irin girman da yake tuna maka akwai wasu 'yan uwa qasa da kai qasa da naka shekarun. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 41 ___________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt ___________________________ "Ni ga tawa tsarabar......Niamey nasan basu da wani abu na musamman da za'a iya tahowa agadez dashi" Ta fadi ba tare data tsaya duba ko tunanin batace komai da ita ba har yanxu. Madarar ta bude ta fiddo wasu qawatattun cups guda biyu ta zuba,sannan a gefan ta saka wani plate din ta shirya fruit din da dukkaninsu take kyautata zaton zabin akhnan ne. Ido ta zubawa plate din sanda falaak ke ajiyeshi kusa da ita. Sai data gansu ta tuna rabonta da abinci tun madarar da tasha da safe a Niamey. Duk wani kayan alatu na ciye ciye da mammina tasa aka bata dare zuwa safiya ana shirya mata ta gaza cin komai. Sultane har abada sultane ne.....akwai shaquwa qauna da soyayya me girma tsakaninta dashi,amma hakan bai canza wayeshi ba,bai canza wannan tsananin nasa da kafiya ba.....bai canza qwarewa wajen iya hukunta mutum ba idan yayi ba daidai ba. Duk da tasani,a yawan lokuta tana cin albarkacin qaunar da yake mata......tana sanyashi ya runtse idanu ya sakar mata abubuwa masu yawa.....Amman haka baya hana wanzuwar d'aci saman harshenta a duk sanda ya murde ya kuma yi wani hukunci. Madarar da falaak din ke miqa mata tabi da kallo. "Karki ce ba zaki sha ba.....kyauta ce daga 'yar uwa zuwa ga 'yar uwarta" Ta fadi tana narke murya da fuska kaman zata saki kuka. Sai bata sake cewa komai ba,ta saka hannu ta karba,ta kai bakinta ta soma sha. Sak irin madarar da tafiso fiye da kowacce,tayi mamaki kadan na yadda akayi falaak din tasan haka,amma izzarta ta hanata ta tambaya. Abun baiwa falaak ciwo ba,tunda har gashi tana sha,tunda har gata a gabanta tana mata fira kuma tana saurarenta,hakan ya sanyawa falaak hope me yawa akan wataran komai zai canza kamar yadda momma keda buri da kuma fata. "Momma nata kewarki......tunda akace kinzo taketa shirin tarbarki,tana ta duban hanya duk da batace komai ba,amma nasan tana jiran ganin shigowarki ne" Falaak din tayi qarfin halin fada. Yadda taga fuskar akhnan din ta gimtse sai taji abun ya tabata,kafin kowannensu yakai ga cewa komai motsin mutum daga baki qofar yaja hankalinsu. Mammina ce ke shigowa a nutse idanunta akan falaak,kafin ta janyesu ta maida kan akhnan sannan ta azasu akan cup din hannun akhnan din,kafin ta kuma saki murmushi tana cewa. "Yauwa......gwara da kikazo ai......ta dalilinki tasha madara kenan?" Mammina ya fadi tana zama gefan akhnan din. Kai falaak ta daga a sanyaye tana duban mammina din kafin ta maida idanunta akan akhnan wadda ta dora kanta a hankali saman kafadar mammina,abinda zai gaya maka zurfin shaquwar dake tsakaninsu. Tsam falaak ta miqe tana ajiye cup din nata hannun. "Zan qarasa ciki yaa biftu......me zance da momma?". Maganar ta saka mammina daga kai ta kalli falaak,shurun akhnan kuma ya zama kusan shine amsa ga falaak,sai mammina tayi murmushi. "Tunda sultane yayi kiranta hankalinta yake a tashe,nayita fama da ita ta shiga ta gaidata amma taxo daki ta wani narke kaman wadda akace yankata zaiyi.....karki damu zasu iya haduwa yanxun nan,don naga jakadiya asabe ta tafi kiranta". Kai falaak ta jinjina a hankali sannan ta juya ta fice. "Ki tashi ki shirya......sultane ya zauna" Maganar data saka akhnan daga kanta babu shiri tana duban mammina. Meye hadin kiranta da sultane yayi da kuma kiran momma da yayi?,hakan na nufin ganinta da zaiyi a gaban momma ne?. Tsaf mammina ta karanci komai ta idanunta,saita girgiza mata kai. "Banaso kiya wani ba daidai ba......banaso ki musanta duk wani abu da nace kiyi". " Indai ni da sultane da ita ne......kiyi haquri mammina......bazan amsa kiran sultane ba" Tayi maganar wani zafi yana tasowa daga qasan zuciyarta. Murmushi mammina ta saki dan qarami. "Harda ni...harni sultane ya kira" Maganar data bawa akhnan relief kenan. Hannunta yana cikin na mammina din sanda suke shiga Qawatacciyar shiyyar sultane din dake da wani irin zubi da ado na daban. Cikin wata doguwar riga ruwan madara ta shirya,wadda qasanta yake a bude sosai yake kuma sharar qasa. Hawa biyu ne da ita,don haka ta saman gabanta a bude yake,saidai an mata wani irin Qawataccen aikin hannu. Daidai bakin dakin hutawarsa jakadiya asabe ta dakata tana ja da baya gami da rusunar da kai,yayin da mammina sukaci gaba da takawa ciki ita da akhnan da takejin zuciyarta kamar zata fito. Bata iya yin sallama ba,sai sallamar mammina data wakilci tata. Cikin muryar sultane ta tsinci muryar momma din,wadda ke zaune daura da tuntum din da sultane ya dora hannunsa dake dauke da ayabar da momma ta bare masa tana kuma yanka abarba taba ajiyewa a plate din dake tsakaninsu. Janye idanunta momma tayi,bata fiya son kallon mammina a tare da akhnan ba,yawan kallon yana qoqarin wargaza mata duk wani kafiya da cijewarta da kuma tsarinta na shekara da shekaru da take tafiya kuma take aiki a kai. "Sannu da aiki" Mammina ta fadi tana zama daura da momma din cikin sakakkiyar fuska me nuna kulawa da damuwa da mutum. "Yauwa" Ta fada tana dauraye hannunta adan wani qoqo na zamani dake gefe ba tare dako ta kalli fuskar mammina ba. Janye ido akhnan tayi daga kansu. Har abada morsa safiyya bata da wani buri illa ta wulaqanta mammina?,akan meye ne?,me mammina tayi mata haka?. Me yasa mammina ba zatayi zuciya ba?,me yasa ba zata haqura ba ta daina damuwa da dukka lamuranta ba?. Tunaninta ya tuqe sanda ta zube gaban sultane tana fadin. "Barka da warhaka bappi.....barka da wannan lokacin" "Yauwa barkanki" Ya fadi a yana dubanta kafin ya janye idonsa daga kanta ransa yana motsawa. "Barka da dare" Akhnan ta fadi tana waiwayawa sashen da momma ke zaune ba tare data kalleta da idanunta ba. Murmushi sosai ya wadata a fuskar momma din,cikin sakakkiyar murya dake nuna kulawa ta amsa. "Barka kade biftu,ina fatan kina lafiya?" "Alhmdulillah". Ta fadi har qasan ranta bataji ita ko kulawarta suna burgeta. "Ya baku taho dukkaninku ba?.....kamata yayi ace dasu aisa din kukazo ai ko?" Ta qarasa maganar tana maida dubanta ga sultane. "Ba buqata,hakanma ba laifi" Ya furta yana turawa akhnan plate din kayan marmarin. Maganar morsa safiyya qwaya daya tak ta d'arsa wani abu saman zuciyar mammina. Nazartarta takeyi kaman yadda zargi me girma ya d'arsu a zuciyar akhnan. Taji a jikinta duk wani kira da sauran b'urbushin fushi da take gani daga fuskar sultane yana da alaqa da momma din. Wai me yasa har abada matar ba zata daina bata ciwon kai ba?,me yasa ba zata daina zama silar bacin rayukanta ba?. A hakanne zata dauki duk wani karatu akan girma da martabarta kaman yadda mammina da sultane sukeso ta dauka?. Abinda ya qara birkita mata tunani shine......hira da sultane ya fara yi shida momma din. Wani abu ya motsawa mammina,ta gyara zamanta cikin sakin murmushi tana jefa bakinta cikin hirar tasu. Bata taba yarda ta zama saniyar ware a gaban sultane,bata kuma yarda da kowanne irin abu yayi mata shamaki ko katanga tsakaninta dashi ba......kamar yadda bata laminci ki na second daya hankalinsa ya juya daga kanta ba. Cikin second biyar kacal sultane din ya jefa tambayar data saka kowacce jijiya tsinkewa daga jikin mammina da akhnan. "Me yasa ba'a shaidamin shirya tseren dawakai guda biyu ba da aka gabatar a Niamey cikin satittika biyu da suka wuce?" Yayi tambayar yana aza idanunsa akan fuskar mammina,tambayar data fita daga bakinsa cikin wani irin calmness hankali kwance,ba alamun fushi fada ko bacin rai,amma kuma cikin qasa da second uku tambayar ta huda qirjinta ta kuma soma yaga bangarorin zuciyar akhnan da tsoro. Maganar tazo mata da wani irin ba zata,ba zatar da bata taba hasashe ba. Cikin ranta taji wannan din shiryayyen abune......wani abu ne da aka shirya faruwarsa,don bataga ta inda maude zai fidda labarin nan ba koda dambunsa za'a yi. Koma dai menene ita din har kullum tana juyawa ne da tsalle a tsakanin lissafinta,bata taba bari wata lamba ko gido qwaya daya ya bacewa ganinta ballantana lissafinta ya shiga rudu. A gaban sultane take,qasqanci kuwa muddin a gabansa ne tayi imanin DAUKAKA ce da kuma cimma nasara me yawan gaske,don haka ta sadda kanta,da muryar ta da tayi matuqar laushi ta fara magana. "Tuba nake......tuba nakeyi ranka ya dade......akwai dalilai da suka......" Hannu ya daga mata. "Ta wuce zaitun....ta wuce,amma akwai na gaba da wala'alla basuzo ba bare su wuce" Sai ya maida dubansa ga akhnan. A lokacin tana jinta ne kamar an tsomata a Kogin qanqara,sai takejin ta gwammace ko wanne hukunci ne sultane ya fadeshi,wataqila ta iya jureshi,wataqila ta samu sassucin fargabar da takeji. "Akwai cikin masu son aurenki da zaki iya gabatarmin dashi a gobe?". Wani gigitaccen abu taji ya dira tsakiyar kanta,ta daga idanunta a birkice tana kallon sultane. Tayi zaton idan ya mata magana zata samu relief ne,ta dauka komai zai soma sassauta,amma sai taji har gwara shurunsa,har gwara baice komai ba. Kai take girgizawa da sauri tana jin wani tashin hankali. Ko kalar wannan tambayar bata shirya amsawa ba bare ita kanta tambayar. "Akwai?" Sultane ya sake tambayarta cikin dakewa yana dage dukka girarsa sama. Ta kasa cewa komai sai kai da take girgizawa. Zamansa ya gyara sosai yana fuskantarta,abu guda daya dake tabbatar mata magana zaiyi kenan da dukka gaskiyarsa. "Ba damuwa bace......ni ina da wanda zan gabatar miki........a gobe ne kuma zaizo......bawai zaizo don ki gane yayi miki ko baiyi miki ba......zaizo ne don ki shaida fuskarsa,ki kuma sakashi cikin mafarkanki na shine mijin aurenki,mijin rayuwarki na dindindin,daga lokacin kina da damar yin tseren dokuna iya dukka adadin gudun da kikeso idan har shi ya lamunce miki". Bata taba yarda zama zai iya gagarar mutum ba sai a sannan. Tana daga zaunen amma neman abinda zata dafa takeyi don ji take faduwa zatayi. "Bappp....." Ta kasa furtawa saboda kallon daya aje mata,saita waiwaya tana duban mammina wadda takejin ita daya ce ta rage mata,itace kawai damarta ya qarshe. Cikin rashin sa'a saita samu mammina din kanta yana a qasa ne tun sanda tayi magana ta farko,kuma har yanzun bata dago ba. Abinda bata sani ba,maganganun sultanate akan akhnan din sune suka qara mata nauyin da takejin kamar ma bazata iya daga kan nata ba har sai an taimaka mata. Wani irin kalar tashin hankali takeji yana sakko mata yana lullube kowanne sashe na jiki da zuciyarta Iya sautinsa,iya kuma yanayinsa kadai ya gaya mata,ko duka duniya zasu taru basu isa su sanya sultane yanjanye hukuncinsa ba a dadai wannan lokacin. Inda kuma akhnan zata fuskanci hakan data hutar da kanta,da bata bata bakinta ba gurin kiran. "Momma......ki taimaka min". Har qasan zuciyarta takejin tausayinta yana narke mata,to amma wata soyayyar wani nuna tausayin wa yaro bashi da wani rana,bashi da wani muhimmanci face jagula komai da yake sakeyi. "Kiyi haquri akhnan......darajarki kenan......mahaifinka bazai taba iya cutar dake ba" Ta furta tana lanqwasa muryarta da zummar ganar da akhnan din,saidai a maimakon ta gane din,sai wani matsanancin jin haushi da jin tsanar momma din ta saukar mata. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 42 ____________________________ *_M&A EGYPTIAN ABAYAS_* *Assalamualaikum* *_Ina dandazon tawagar gayyar MATA 'YAN QWALISA?_* *_WADANDA SUKAYI AMANNA DA ADO SUNE MUTUNCIN D'IYA MACE?_*👘🥻 *Ina masu son sari ko siyan daya na Egyptian abaya masu quality su iso garesu cikin Aminci???* *M&A EGYPTIAN ABAYA itace zabinku NA FARKO* *kuse ABAYAS takanas kuma kai tsaye DAGA EGYPT su iso gareku cikin kasa da kwana goma KACAL!✌🏽* *_Ina masu son siyan abaya Amma Kuma basuda halin siya lokaci daya?_* *_zaki iya ringa biya ahankali har ki kammala abaki abayarki cikin aminci_*🙌🏽 *Sannan gamasu San siyan airfreshener a farashi mai sauki muna dasu* *muna turo da mayukan kitso original AMLA da VATIKA* *Idan kana da wani personal shopping dakakesan ayi ma duk munayi CIKIN QASAR EGYPT da yardar Allah* +20 114 341 0873 ko kuma 0810 959 7791 https://chat.whatsapp.com/Hm9HBCXeyfjFDwi3OPSFqP?mode=wwt _____________________________ ★Sai data tattara dukkan wani qarfin halinta da qwarin gwiwarta sannan ta iya kiran sunanta. Daga inda take zaunen,gurin da tunda suka shigo dakin ita da mammina din bata iya motsawa daga gareshi ba. Tana jin gangar jikinta ne kaman ba'a liqe take da ruhinta ba,infact tana jin gangar jikinma gaba daya kamar ba tata ba. Abinda kawai zata iya banbancewa shine,yadda tafukan hannayenta dama na qafafunta suka dauki dumi,kaman yadda taji fuskarta tana wani irin huci ita kadai. Tana sake maimaita da nanata zantukan sultane ne kawai.......a taqaice dai abinda sultane yake nufi shine.......yayi mata miji?. Kaman an doka ganga tsakiyar kanta sanda lissafinta yazo a nan. Tana jin komai ne kamar almara.......a ra ta takeji wannan abun bame yiwuwa bane. Bada ita ga wani kamar kyautar kofin shayi?,bada ita ga wani mutum da batasan meye mataki ko darajarsa ba arayuwa?. Wai waye wannan ma wanda zaiyi ganganci nutsar da rayuwarsa cikin nata?,waye shi da har ya samu wannan galabar a taqaitacce lokaci?,yake nema raba soyayyar dake tsakaninta da sultane?. Yin wasan tseren doki kadai shi zaisa sultane yanke mata wannan hukuncin da yake daidai da mutuwarta?. Ina qaunar da sultane yake mata?,ina soyayyar da yake mata gaba daya ta tafi saboda kuskure daya tak?!. "Biftu" Mammina ta furta tana qoqarin hadiye abinda yake mata kai kawo tana zama a gaban akhnan. Da qyar ta daga idanunta da suka sauya launi,wadannan kyawawan blue eyes din da suka jirkita zuwa launin ja,ta zubawa mammina su ba tare data iya cewa komai ba. "Ki nutsu ki kwantar da hankalinki........sultane bazai miki auren dole ba". Wani murmushi da sam bashi da nasaba da dangantaka da halin da take ciki ta saki,ta zauna sosai daga sunkuyon da tayi tun a dazun. "Ba sultane ba mammina......ni da kaina bazanwa kaina auren da banaso ba......bazan yi musu da sultane ba,bazan kuma bijire masa ba.......amma ina me miki rantsuwa,ko waye zaizo a goben sai ya kwashi kashinsa a hannu,zan sakashi ya banbance tsakanin aya da tsakuwa......saina sashi yaji nadamar yunqurin neman auren gimbiya khadeeja akhnan......wannan alwashina ne" Tana kaiwa nan ta miqe,duk da a zafi take amma yanayin tafiyar nan tata mai cike da qasaita bai sauya ba,ta nufi dakinta kai tsaye tana shirin maida qofar ta kulle mammina na qwala mata kira. A yau kam ko mammina batajin zata tsaya jin abinda zata ce mata.......kwanyarta ta cika da dimbin tunanin WAYESHI?. Me ya taka?,me kuma yake taqama dashi?,yasan wacece ita ko kuwa ganganci kawai zai gwadawa rayuwarsa?. Idanun mammina akan qofar har zuwa sanda akhnan ta bacewa ganinta. Dauke dubanta tayi daga wajen,ta sauke hannuwanta ta soma takawa tana barin wajen. Ba haka take so ba.....zamanta a daki ita daya zai sanya ta qulla wani tunanin na daban da bashi ya cancanta yazo kanta ba,tana buqatar zamanta a kusa da ita......a daidai wannan lokacin bai kyautu ba bai kuma kamata ta zauna ita daya ba,sai ita kanta tana buqatar kebewa,tana buqatar ta kebe ita daya,kebewar da zata kasance daga ita sai numfashinta kadai,wataqila zatayi wani tunanin daya kamata ya kuma dace da ita. Wani irin birkitattun tunani ne suke zuwa kanta sanda take shiga qasaitaccen bedroom din nata,ta kuma maida qofar ta kulle. "Anya bazan makara ba?" Ta furta a hankali tana dora yatsanta saman labbanta. Takawa taci gaba dayi tamkar me tsoron taka qasa. Kai tsaye ta nufi wata qofa da yanayinta da adon jikinta yasha banbam da sauran qofofin dake maqale a dakin. Murzata tayi sannan ta turata ta shiga ciki. saika shiga sannan zaka fahimci ma'adanar suturu ce,wadda tafi kama da katafaren shagon siyayyar kayayyaki na zamani. A hankali take kutsawa ciki,tana ci gaba da ratsawa harta isa sassan da atamfofi ke ninke,wasu kuma a saqale jikin hanger. Hannu ta saka ta turesu gefe,ta sanya hannun nata qasan ninkakkun atamfofin ta ciro wani qaramin muqulli,sannan suma ta sake turesu gefe,take wani alamu kaman tsaga ya fito daga ainihin ginin katakon da kayan ki shirye wasu a maqale a jiki. Muqullin takai jiki,wanda a haka ba zaka taba cewa akwai wani gurbi da za'a iya zura muqulli ba,take ya shige,tayi murxawa uku sai ga wata qaramar ma'ajiya ta fito. Hannunta ta miqa,a miqawar farko kuma ta fiddo wani file,saita maida qaramar qofar ta kulle sannan ta dawo da baya ta dawo ainihin dakin suturun. Saman wani babban tuntum ta zauna,wanda takan zauna a yawan lokuta idan ta fito daga wanka zata shirya. Dora file din tayi saman cinyarta,ta ware wani zare da aka daureshi dashi. Koda ba'a gaya maka ba,a kallon farko idan kayi masa zaka fahimci tsohon file ne daya kwashe adadin wasu shekaru,tun daga yanayinsa da yanayin takardun ciki kawai zasu gaya maka hakan. Ci gaba tayi da karanta takardun daya bayan daya,har zuwa sanda tazo kan wata takarda dake manne da wani hoto. Hoton ta zubawa idanu tana kallo sosai,sannan a nutse ta maida dubanta kan adress din dake qasan hoton tana karanta rubutun. "Anya ba yanzu bane lokaci yayi?......anya lokaci baiyi ba" Ta dinga nanatawa ita da zuciyarta kadai. Zataso ace akwai wani a gefanta.......zataso ace akwai wani a kusa da ita da zai gaya mata EH ko A'AH,wanin zai bata tabbacin lokaci yayi ko baiyi ba,saidai wannan din wani babban ajiyayyen sirri ne da idan ka dauke zuciyarta dake rayuwa a qirjinta tun daga haihuwarta har kawo yanzu.......bata tunanin akwai wata halitta ta daban da tasan dashi. Ajiyar zuciya me nauyin gaske ta sauke,tana kuma fesar da iskar hunhunta daga bakinta. "Lokaci yana dab da qarasowa......taku daya zuwa biyu kacal ya rage" Taji tana gayawa kanta da kanta. "Dagin qafa gwaya daya tal tana iya zubda kowacce dama.......kubucewar dama daga hannun dan adam ba wani abu bane me wahala.......wannan din wani karatu ne data jima da haddaceshi,wani karatu ne daya zame mata babban darasin rayuwa,darasin rayuwar kuma da har yau yake kan biyashi,ba kuma zata sake kuskure ko yarda da qaddararta ta ninku sau biyu ba. Agogon cikin dakin nata ta kalla,daga rana irin ta yau tana jin ya kamata ta haramtawa kowa shiga dakin sai ita daya,koda kuwa yalwa ce. Daidai lokacin da agogo ya buga mata qarfe sha daya daidai na dare,sai ta taka a hankali zuwa saman dressing table dinta,ta sanya hannunta ta dauki wata qaramar waya da alamunta suka nuna nan ne gurin zamanta na dindindin,ta soma laluben lambobin wayar tamim. Bugu daya tak aka daga wayar daga bangaren da tayi Kiran "Akwai wasu abubuwan da suke buqatar gaggawa gurin sanyasu a gurabensu da kuma muhallinsu......wasu abubuwan nawar yinsu takan iya zama babbar illa da zai zama sanadin rugujewar komai......awa daya mai zuwa......ka hallara a gurbinka". " An gama ranki ya dade" Abinda yace da ita kenan,tun kafin kuma ya ajiye wayar ita ta kasheta,ta maidata inda ta dauko ta ajiyeta,sannan ta yiwa file din hannunta kyakkyawar ajiya,ta taka zuwa bakin qofa ta murza tana fita a dakin. ★★★Daga saman tableware din dake shimfide a qasan dakin cin abincin momma na zaune tana kallon yadda falaak ke shirya komai a wani kyakkyawan kwando,yau din da kanta da hannunta,duk da cewa dama can ita din bata dauki qananun hidimawa kai irin wannan a wani abu me girma ba. Bata dogara da komai sai hadimanta sunyi ba,kafin suzo suyi wani abun ita tuni ta kammala abinta. Da murmushi a fuskarta ta juyo tana kallon momma. "Ku cika alqawari.......domin shi alqawari abun tambaya ne......zanje naga yaa biftu,nakai mata gift din safe" Idanu momma ta lumshe tana jinjina kai. "Amma kuwa zaki samu ganinta a yau dinnan?" Momma din ta fadi. Ba ita ta raini akhnan ba......bata kuma tashi a tsakanin hannuwanta ba,amma ta tashi a cikin zuciyarta. Bata kwana da akhnan ta tashi da ita ba,amma tana qididdige da dukkan halaye da kuma dabi'unta. Batajin a dukka halayenta akwai wani baqo guda daya,bata tsammanin zata kasa sansano wani dabi'a tata. Jini ba wasa bane,tayi imani yana da qarfin ikon yin abinda zato bai taba zato ba. "Zanje koda bazan ganta ba.....ai nasan zatasan naje ganinta......amma momma" Falaak ta fadi tana gyara dankwalin abayar kanta dake shirin zamewa saboda santsi. "Tunda tazo.....bata shigo ta gaidaki ba" Ta fada a sanyaye tana duban momma. Murmushi ta sake sakin mata tana girgiza kai. "Idan zakayi abu kayi domin Allah....domin shine taka ribar a duniya da lahira.......banaso ki fiya zurfafa bincike,banaso kuma ki fiya zurfafa bin qwaqwaqwafi akan alaqa da dangantakar dake tsakanina da biftu......tsakaninki da ita daban,tsakanina da ita daban" Shuru tayi maganganun momma suna neman gurbi da muhallin sauka cikin zuciyarta,saita jinjina kai,ta sanya hannu ta dauki kwandon tana yiwa momma sallama. Duk wanda ya tareta cikin hadiman da zummar karbar kwandon a hannunta saita dakatar dashi. A haka har ta cimma sassan mammina din,bakinta dauke da sallama. Cak mammina ta dakata daga kai chips din bakinta,ta sauke spoon din tana duban falaak dake takowa ainihin falon daya zama kebantacce. Ba kowa bane yake da ikon shigowa wannan shiyyar ba sai wanda mammina din ta amincewa,yarinyar ta shigo ba tare da an sanar da ita shigowarta ba. "Tana jin cewa jinin sultane ce ita......ta cancanci shiga dukkan wasu iyakoki da sauran mutanen gidan basukai su shiga ba". Wannan batun ya saukar da murmushi saman fuskar mammina,ta haqura da cin chips din,ta soma marabtar falaak din da fadin. "Yar uwa tazo ganin 'yar uwarta,yau ma dai kaman jiya,bansan me tasa a cikinta ba,har na gaji da magana tacemin ta qoshi,ban sani ba ko zuwanki zai sanya taci wani abu" Mammina ta fadi tana yiwa hadimarta dake tsaye a gurin magana taje ta kira akhnan. Mintuna a qalla uku barira ta dawo,kanta a qasa take shaida mata. "Nayita taba qofar amma ko magana batayi ba bare ta tambayi ba'asin bugawan". (08187255862 lu'u lu'u paying) " Koma ki sake taba qofar kice tazo injini" Mammina ta fadi tana duban barira. A tsorace barira ta sauka tana komawa,dukka ba'a son ranta ba,tayi ne kawai don cika umarnin uwar gijiyarta,don bata da tabbacin meye zai faru idan har taci gaba da buga qofar akhnan din. "Idan kikayi kuskuren sake zuwa kika bugamin qofa......ki tabbatar zaki hadu da fushina" Iya abinda tace da ita kenan ba tare data damu da sanin waye yake buga qofar ba. Idanunta ta janye tana jan wani dogon tsaki kamar ta tsinke harshenta,saita maida kanta kanta saman pillow din ta kwantar,taja wayarta taci gaba da buga game dinta,tana kuma ci gaba da irgen awannin zuwan ME GANGANCI HADE DA KUSKURE sunan data sakawa baqon da bata damu tasan koda sunanshi ba. Kai a qasa barira ke maimaitawa mammina abinda akhnan ta fadi,ta kuma qarashe da fadin "Ki gafarceni". Kai mammina ta gyada a hankali tana fesar da iska. Mamaki ya kama falaak......sai ta miqe kawai,mammina ta bita da kallo. " Kiyi haquri da halayyar 'yar uwarki,kada kice zakiyi fushi,tana da kafiya da taurin kai......dabi'unta sunsha banban da wadanda kika saba gani". Murmushi falaak ta saki tana rolling mayafin abayarta a kanta. Ita sam bataga ma dalilin da zai sanya sai anyi mata iso gurin akhnan nan. 'Yar uwarta ce fa?,jininta kuma. "Ba dalilin da zanyi fushi da ita mammina.....ko yaya take......ko me tayi hakanan nake qaunarta,jinina ce,bani da kamarta ballantana sama da ita" A nazarce mammina ke kallon falaak sosai tana kuma sakin murmushi. "Dauka mata kwandon barira" Ta furta tana duban falaak din still. Kai ta girgiza tana sunkuya ta dauka. "Zan iya mammina.....saina fito,na gode qwarai da karamci" Ta qarasa maganar tana nufar hanyar da zata sadata da dakunan. Da kallo mammina tabi bayan falaak din. Tana iya tuna yaushe aka haifi falaak,a nata idanun kamar yau ne......amma gashi a yau din ta zama mutum,tama zama cikakkiyar budurwar da zaka dauka tafi qarfin shekarunta goma sha bakwai,saboda yanayin cima da gata da kuma kulawa,uwa uba kuma nutsuwarta saita sanya kaman tafi qarfin shekarunta. Anya kuwa iya wannan abun data gindaya ya isa?,ya isa kuwa?. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 43 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ____________________________ "Falaak ce ke neman izininki......wannan falaak din guda daya da jininku ya kasance iri daya sak da sak" Lafuzzan falaak din da suka shiga kunnenta kenan sanda ranta ke kaiwa qololuwar baci jin an sake buga mata qofa,bayan dukka gargadi da jan kunnen da tayi,sai kawai ta danna remote din dake gefanta,hakan ya bawa qofar damar bude kanta da kanta ba tare data tashi ba,wannan ya bawa falaak daman tura qofar dakin ta saka kanta ciki. *BAYAN AWA UKU* Idanunta da dukka nazarinta yana kan akhnan sanda take shigowa dakin. A tausashe tayi mata sallama,abinda ya sanya akhnan din daga kai daga kan system dinta tana duban mammina din. Duban second uku tayi mata,sannan ta motsa labbanta tana amsa mata gami da janye qafafunta da kuma kallonta daga kan mammina din. List din sunayen ma'aikatan da aka dakatar daga sahel couture take dubawa,neesha ce ta tura mata tana neman samun tabbaci daga gareta. Batasan sanda akayi korar ba,batasan kuma dalilin korar ba. Dukkanin mutanen a iya saninta ba wanda aka taba kamawa da wani laifi na cin amana ko zamba cikin aminci,hasalima suna aiki dasu ne tun kafin kamfanin ya koma hannunta kuma mallakinta. Wasu daga cikinsu ma su suka tallafi rauninta zuwa sanda tayi tsaiwar daya kamata ace tayi din. Sauke idanu mammina tayi akan kwandon da falaak ta shigo dashi a wannin baya. Yana na a gurin,ga kuma kayan ciki da aka fito dasu da alama anci wasu abubuwan a ciki. "Wasa wasa nima tawaye akeson yimin kenan?" Ta kasa jurewa ta fada tana zama gefan akhnan,saidai kuma fuskarta tana qunshe ne da murmushi. Idanu akhnan din kawai ta zuba mata,abinda ya alamtawa mammina bata fahimta ba,neman qarin bayani takeyi. "Eh mana......falaak na neman qwacemin ke cikin kwana biyun nan,nawa abincin ya zama hoto" Qoqari tayi tadan sassauta fuskarta,saita dauke hannunta daga saman system din tana gyara zamanta,abunda ya danja hankalin mammina kenan "Mammina.......akwai wani abu da akayi ne game da sahel couture?" Kai mammina ta jinjina a hankali,idanunta cikin na akhnan "Akwai......kuma ban gaya miki bane saboda yanayin da kike ciki,jira nake ki samu nutsuwa tukunna sai mu zauna nayi miki bayani" Shuru kadan akhnan din tayi,tana jin abun wani daban a ranta,saboda wannan din shine canje canje na farko da aka fara yi cikin kamfanin,tunda ta karbi ragamar tafi dashi shekara kusan hudu kenan. Ba wani abu data gani wanda zai sanya ayi buqatar canza komai,to amma batasan me mammina din ta hango ba. Idonta ta mayar ga fuskar mammina din,sannna ta gyada kanta a hankali. "Ki tashi buhaina zata shigo ta shiryaki" Mammina ta fadi tana duban fuskarta. Jim tayi tana duban mammina din,da tarin mamaki kan fuskarta,saita jinjina mata kai. "Eh,lokaci yana qara tafiya idan da kin duba agogo.......gwara ta shigo da wuri ku kammala da wuri" Sake zubawa mammina ido tayi,takaici yana kamata. Wannan mutumin wannan baqon da batasan wayeshi ba......batasan meye capacity dinsa ba shine zaa tsaya shiryata a kanshi?. Ta gaji da wannan walagigin da akeyi da ita na babu gaira ba dalili. Na meye zata dinga bata lokutanta masu muhimmanci saboda zuwan wani gareta?. Dauke idonta tayi daga kan mammina din,tana jin bata aminta ba,bata kuma gamsu ba,hakanan bataga dalilin da zai sanya a bata mata lokaci saboda wani ba,saita fara kashe system dinta. "Akhnan" Mammina ta kira sunanta da wani yanayi,ta kuma kira sunanta da sunan da ba kasafai ta fiya kiranta dashi ba. Manyan lumsassun blue eyes dinta ta daga tana duban mammina din. "Ba don shi ba..... Saboda ke,saboda darajarki,saboda martabar da kike da ita. Kinfi qarfin kowanne namiji ya kalleki ba tare da ado na qasaita a tare dake ba,ba abinda ke qarawa mace kwarjini irin ado......adonma da sarauta ta bata ta kuma baki kema.......ba donshi bane akhnan " Shuru tayi tana juya maganar mammina a ranta. Kamar yadda ta tsani FADUWA haka ta tsani aga kasawarta......kamar yadda take ji da duk wasu martabobi da darajoji nata hakanan take fatan riqe wannan martabar tata,kawai saita maida idanunta qasa,bata sake cewa da mammina komai ba,kaman yadda bata sake musa mata ba,abinda ya bawa mammina tabbacin ta sauko daga dokin naqin da tahau. "Bana buqatar wani shiri me nauyi,shigar dana saba irin ta yau da kullum kawai" Ta fadi a nutse da wani irin izza,daidai sanda mammina ke hanyar fita a dakin. Murmushi mammina tadan saki tana kada kai. "Koma dai meye.....kawai ki girmama ra'ayin mahaifinki". Tace da ita sannan ta juya tana fita a nutse. Sai da mammina ta fita din sannan ta daga kanta anutse tana duban hanyar da tabi din. Fashin baqi takeson ta yiwa lafuzzan mammina,ta girmama maganar sultane?.....kodai mammina na shirin goyon bayan ra'ayin sultane da morsa safiyya ne?,matar da dukka zatonta yake gaya mata da dukka shirinta da kuma masaniyarta aka qulla mata komai. Janye idanun nata tayi sannan ta miqe a nutse,har cikin ranta batajin akwai wani dalili da zai sanyata ta janye ra'ayinta ko ta amshi wani d'a namiji a yanzun cikin rayuwarta,koda akwai yiwuwar hakan saidai nan gaba. A yanzun bata shirya rayuwa qarqashin umarnin kowa ba......bata shirya rayuwa qarqashin tilastawa da zabukan da suka kasance na wani ba,abinda ta sani shine 'YANCINTA.....DUNIYARTA.......KUMA RAYUWARTA. ★★Tun daga saman fuskarsa zuwa shigarsa kadai zaka iya hangen tarin wani irin ajiyayyen kwarjini. Wani irin kwarjini na musamman dake cakude da kwarjinin jinin sarauta dake zagaya masa da kuma tarin haske da nutsuwar da ilimin addini yake shimfidawa saman fuskar mamallakinsa. Sanye yake da wata cloak robe da aka saqata da wani irin tattausan yadi me dan sheqi sheqi......sheqin da zai gaya maka tun daga auduga zare da kuma saqar da akayi mata me tsananin daraja ce. Riga ce da yawancin manyan malamai na larabawa......manyan malamai na harami sukan sanyata,irin rigar da kake hangota me zubin abayar mata daga jikkunan attajiran larabawa. Fara ce,saidai ba fari qal baa,wadda aka yiwa aiki da gold din zare daga gabanta zuwa hannuwanta. Jubah ce a ciki wadda da yawa mukafi kira da jallabiyyar maza,saidai wannan din ta musamman ce da tasha banban da irin jallabiyyar da sukafi yawa a gurarenmu,don wani irin qawataccen dinki akayi mata. Iya wuyan rigar da hannun kawai ka kalla zakasan tasha banban da sauran jallabiyyu,hannun da lafiyayyen agogon rolex daya daura masa ya sake zama wani ado na daban gareshi,ya kuma dace da zoben azurfa me sheqi qwaya daya dake tsakiyar yatsarsa. Rawani ne me kyau daya zauna saman kansa,ya kuma fitar da anihin sassanyan kyan nan nasa,ya zauna a kansa,banda jelar rawanin data sauka kafadar hagunsa zaka dauka wata sabuwar plain cap ce da tazo tare da cloak robe din jikinsa. Wani half shoe ne a qafarsa daya kwanta ya kuma dace da yanayin shigar tasa na asalin fata qirar kamfanin qasar Italian. Su uku ne tare dashi,abdii yana a gefan damansa,hamdi yana daga hannun hagunsa,sai Maher daya kasance sanannen dan gari. Tun daga nesa kadan motarsa qirar Mercedes AMG g63,wanda zuwansa agadez ya siyeta da tarin daloli masu yawa. Salawi ne yayi driving nasu,saidai kusan tazarar taku d'ari ya tsaida salawi din. "Ka koma gidan,idan na kammala mu sake haduwa a nan ka maidani gida". Ya furta yana sanya hannunsa saman murfin motor zai bude,saidai kafin yakai ga budewar har hambal ya zagaya ya bude masa cikin matuqar girmamawa ya kuma ja baya yana jiran fitowarsa. Sanda yake fitowa beeno ya soma gyara masa zaman cloak robe dinsa,ya daga kai a nutse ya sauke masa wani kallo daya saka hantar cikin beeno din kadawa. Baya yaja yana sadda kanshi,ya mace da irin nasa tsarin,sam sam irin wadannan al'adun basu sha mishi kai ba,hasalima ba sonsu yake ba,to amma shi din amanarsu ne,da kuma umarnin mooti suke aiki,dole ne su bashi dukkan wata kulawa data kamata,su kula da dukka motsinsa da lafiyarsa koda ba kai tsaye ba don sauke amanar adalin sarkinsu mooti abba jifar. "Of eeggannoo godhaa....hin irra deebi'iin(ka kula....kada ka sake maimata hakan)" Ya furta da yaren oromo yana dauke brown eyes dinsa da hasken rana ya sake maidasu wani launi me fusgar hankali. "Am dhiifama...Dhiifama naaf godhaa(kayi haquri,ka gafarceni)" Ya furta yana ja baya. Abdii ke binsa da kallon mamaki,yanason magana amma kuma yadda sukayi da beeno ya sanyashi sawa bakinsa sakata. Wacce rayuwa *PRINSII SHEIK MUHAMMAD HAISAM ABBA JIFAR* ke shirin yi a agadez?. Rayuwa ce irin ta kowanne mutum me matsayi daidai dana dan uwansa......ya manta waye shi wai a qasar jimma da Ethiopia gaba daya?. Har yanzu da suke dab da SULTANE PALACE yana jin wani fargaba. Kada dai yaje yace zaiyi rayuwa irin ta qasqantattun mutane?. Idan hakan ya kasance anya zai iya jurar gani kuwa?,zai iya cin amanar nanay da sultane ba tare da ya gaya musu ba?. "Ku koma......zamu shiga ne da iya Maher" Ya bada umarnin na kai tsaye,wanda a take dukkansu sukaja baya,banda abdii da yayi tsaye cak a wajen. "Maaloo....(please)......." Abdii ya fadi yana duban bayan haisam da sukaci gaba da takawa shi da maher zuwa babban katafaren qofar gidan. "Andii!" Yadan kira sunanshi a kausashe ba tare daya waiwayoshi ba. Duk yadda abdii keson ya bisa bazai bar shi ya soma taka gidan yanzu ba,zai iya wargaza komai,don ba lallai yaga an masa ba ya iya dauke kanshi kaman ba kowa ba. Koda zai fara shiga da abdii ba yanzu ba,sai yayi masa kyakkyawan training da bazai sauka daga qa'ida ba. Daya bayan daya suke wuce sassanni da shinge shinge na gidan,har zuwa sanda suka fara shiga hurumin jinin masarautar kadai da na kusa dasu da kuma wadanda aka yarjewa. Babbar qofa ta qarshe daya daga cikin hadiman morsa safiyya ya qaraso,a bayanshi mutum uku ne da duka marabci haisam din. "Zamu fara yin sallah tukunna" Ya amsa musu yana duban agogon hannunsa. "Babu laifi.....me martaba yana buqatar ganawa dakai dama kafin soma zaman karatun.....shi dinma yana a masallacin". Kai ya jinjina kawai,ya kuma nemi su masa jagora zuwa cikin masallacin. Akwai ragowar lokaci,don haka ba cika sosai a masallacin,uwa uba kuma me martaba da yake ciki yana ganawa da wasu baqin. Ganinsu tare da hadiman morsa safiyya ya sanya basu samu wani wahala ba,dakarun dake tsare lafiyar sultane din cikin shigar kayan sulke suka dinga janye manyan gororin hannunsa da mashi suna basu hanyar wucewa,daga nan har zuwa ainihin cikin masallacin. "Iyakacinmu nan.....amma kai kana iya shiga,lokacin shigarmu baiyi ba yanzu" Suka fada suna dakatawa. Idanunshi kawai ya dauke a kansu,sannna ya juya a nutse da zummar zare half shoe din qafarsa. Da hanzari ya murxawa Maher yatsuntsa guda biyu,abinda ya sanya Maher din saurin tashi daga duqawar da yayi ya zummar zare masa takalmin (08187255862 lu'u lu'u paying) "Hin dagatinaa" Ya masa magana da yaren oromo qasa qasa,ta yadda yayi imanin babu me fahimta koda yaji,sai ya tsaya qyam yana daidaita nutsuwarsa,kafin su taka a tare suna shigewa masallacin. Wani irin katafaren masallaci ne me wani irin girma da kuma daukan hankali. Tun gabanin su shiga cikin masallacin haisam din ya gama karantar yanayin gininsa,gini ne da yake nuna zallar qwarinsa da kuma hikima sosai gurin ginashi. Duk da yaune karon farko da yayi ido da ido da masallacin me tsohon tarihi,amma ya jima yana haduwa da rubuce rubuce a kansa. Abinda yafi bashi mamaki shine maganar bawa Allahn da ya zama jagoran ginin masallacin wato mallam zakariyya daya bada tabbacin duk wanda yaga faduwar ginin masallacin,to ba shakka zaiga tashin qiyama. Ba wani abun mamaki bane gane me sarauta daga jinin wani masaraucin,musamman ga nutsatsen mutum ne tsananin tsinkaye da dogon tunani da kuma hangen nasa irin haisam din. Sultane din na dabanne......kamar yadda kwarjininsa ya zama wani na daban. Saman wata qawatacciyar shimfidar dake nuna asalin sarautar qasar agadez din yake zaune. Yasha ado da launin kayan da suka kasance koraye ne,irin launin koren dake da daukan hankali da idanun me kallo. Daga hagunsa da kuma damarsa mutane ne zaune,mutanen da kana kallonsu kasan akwai kusanci tsakaninsu daya basu daman zama haka su dashi,sai kuma alamun dake nuna akwai magana me muhimmanci da suke tattaunawa. Sarkin fada ne ya motsa,cikin tausasa harshe yake sanar da sultane isowar haisam din,abinda yaja hankalin sultane din a nutse ya daga idanunsa zuwa ga haisam wanda yake tattakowa cikin nutsuwarsa. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 44 Gauraya idanunsu sukayi guri guda,,idanun sultane muhammad hammud a kansa,yayin da haisam ya janye kallonsa daga kan sultane,saboda dabu'antuwa da yayi na rashin girma ga sanya ido cikin idanun manya. Amma a qasan ransa yakejin wani nauyin mutumin,mutumin da yau ne karon farko daya soma ganinsa ido da ido,duk da baisan adadin iya hotunansa daya kalla ba a sanda bincike ya biyo dashi ta qasar a sanda yake shirye shiryen tahowa agadez din. Daga inda sultane yake zaune yana nazartar tahowar haisam din,cikin jikinsa yake jin wani abu na daban game da yaron. Baiyi tsammanin ganinsa haka ba,matashin dake da qananun shekarun da duka duka basufi talatin ba zuwa da uku,ya dauka wani babban mutum ne zai dauki jagorancin karatunsu falaak din. A nasa son yafison me shekaru,to amma hakanan cikin jikinsa karon farko yakejin ya aminta da yaron. Cloak robe dinsa yake qoqarin tattarewa don duqawa yakai gaisuwa ga sultane. Yadda yakeyi din kadai yasa sultane yakejin kamar ya dade cikin masarauta,sai ya daga hannu yana dakatar dashi daga qudawar da yake shirin masa,maimakon haka hannu ya bashi direct,haisam ma kuma ya miqa masa nasa sukayi musabaha,sannan sultane ya masa masauki kusa dashi. Mamaki kadan ya d'arsu a zuciyar mutanen dake gurin,duk da cewa sultane din mutum ne me karamci qwarai,yana da girmama mutane sosai,babu ma kamar ace mutum masanin addini ne......kuma mahaddacin alqur'ani,wannan girman nasa yana ninkuwa a idanun sultane din. Cikin nutsuwarsa yake bin tattaunawar da sukeyi akai,sai a sannan ya fahimci akan wasu dokoki ne na shari'a da akeson fiddasu,da wasu boyayyun qa'idoji na shari'a da za'a yisu a rubuce,ayi kuma seminar ta kwanaki ana wayarwa da malaman qasar agadez din kai. Takardu aka raba a gurin,har tazo kan haisam. Idanun sultane a kansa sanda yasa hannu ya karba,ya bude ta a hankali yana duba maudu'an da suke ciki,da bayanan da ake buqatar warwaresu. Murmushi kawai ya saki a nutse,ya maida takardar ya ajiye yana dora idanunsa akan sauran malaman da suke gurin. "Ko zaka warware mana kowanne hukunci?" Muryar sultane ta sauka a kunnen haisam. A nutse ya waiwayo ya dubi sultane cikin girmamawa,a kallon farko kuma ya fahimci wani gwaji ne sultane yakeson masa. "In fada tana da buqatar hakan sai nayi ranka ya dade" Ya furta da sasanyar nutsuwarsa cikin girmamawa. Kai sultane ya gyada yana dauke idonsa daga kan haisam,murmushi kwance qasan zuciyar sultane din. 'Yan qananun mintunan da yayi da yaron ya fahimci yana da wata irin tarin nutsuwa da kuma kwarjinin da ba kasafai aka fiya samunsa jikin kowanne mutum ba,irin kwarjinin da yafi fita ne daga jikkunan ahalin sarauta. Cikin qwarewa da tarin baiwar fasaha da zalaqar zance haisam din ya soma bayani da sharhi,bayanin da yaja hankalin duk wani wanda yake gurin,ya kuma sanya sultane maida hankalinsa kacokam kan haisam. "Bari mu fara da hukunce hukuncen dake kan bayi mata......baiwa a daraja da martaba ba kamar d'iya take ba.......idan 'ya zatayi idda wata hudu da kwana goma,to baiwa wata biyu zatayi da kwana biyar shine iddarta.......,idan baiwa tayi zina,istibara'inta zai kasance haila daya ne wato jini daya,idan aka saki baiwa zatayi idda na wata biyu ne,ba kamar 'ya da zatayi wata uku ba,idan me baiwa ya siyar da ita ga wani,jini daya nan ma zatayi kafin ta zama mallakin wancan,sauran abinda ya shafi 'ya shine kamar haka. Duk wanda yayi zina da mace,sannan aka daura musu aure kafin tayi istibra'i to wannan auren batacce ne ba halastacce ba,dole a raba wannan auren,idan kuma har ya kebe da ita to taci sadaki,dole ya biya sadakinta,bayan ta gama istibra'i bayan rabuwarsu yana da ikon sake aurarta halal ne......" "Amma kuma duk wanda ya daura aure da mace tana cikin idda,sannan ya tare da ita,to aurensu ya haramta har abada,koda ita dashi ne kawai suka rage a duniya,kwatankwacin hukuncin ma'auratan da sukayi li'ani(tsinenenuwa),ya rantse d'an data haifa ba nashi bane,itama ta rantse d'anshi ne,to bayan sunyi haka a kotu a gaban alqali wannan aure ya rabu har abada,kuma sun haramta ga juna har abada" Numfasawa yayi a hankali sannan yace. "Iddar qaramar yarinyar daka saki,wadda bata fara al'ada ba,watanni uku zatayi kaman yadda babbar mace zatayi,sannan iddar me kwantaccen ciki.......". Sake daukan shuru masallacin yayi,yayin da dukka fuskokinsu ke gaya masa yadda bayanin nasa yake shiga. "Mace me kwantaccen ciki shekara hudu ne,zatayi shekara hudu sannan ta sake wani auren" "Allahu akhbar" Sultane ya fada a hankali yana girmama lamarin shari'a,tabbas ita din sabanin hankali ce. "Wadda ta debe tsammani da ganin haila,saboda shekaru itama watanni uku ne iddarta.....kaman wadda take shayarwa,wadda bata haila sanadiyyar shayarwar,to iddarta zata kasance shekara guda,hakanan macen da bata da cikakkiyar lafiya,itama shekara daya ne iddarta.....macen da take cikin jinin cuta wato istihadha,itama iddarta shekar daya ce". Ya qarasa fada a nutse yana sauke muryarsa qasa. "Ma sha Allah.......ma sha Allah" Sultane ya samu kanta da furtawa. Duk wanda yake gurin saida bayanan nasa sukayi masa dadi. Shugaban malamai ya motsa kadan yana duban sultane. "Allah ya taimakeka,dukka ya tattara bayanin ya gama yinsu,abinda kawai ya rage shine rubutasu a tsare,aka rarrabasu zuwa guraren da suka dace". " Zaka iya tsarasu a rubuce?" Sultane ya maido dubansa ga haisam. Nutsatsen murmushi ya saki,a duniya baya ga bincike da rubuce rubucen addini ba wani abu da yakeso yake kuma masa dadi gami da qawata lokutansa,sai kuma aikinsa na intelligence da yakeyi. "Ba zaya gagara ba in sha Allah,hukunce hukunce ne daya kamata a sansu a kowanne gida,kowacce mace da kowanne magidanci susan dasu,saboda wadannan sune hukunce hukuncen da suke tsaftace aure,kowa ya sani daga aure ake samar da zuri'a,zuri'ar nan me kyau ko maras kyau?. Yadda za'a tsaftace mahaifa don samun 'ya'ya daga bayyanannen tsatso kuwa yana da nasaba da samar da 'ya'ya na gari,da yawa an haifi yaran da nasabarsu ta cakuda data wasu......an haifi yara cikin iddar auren wani,an daura aure cikin sauran haqqin wani mijin,wannan sai yake zama sanadin haifar yaran da suke gagarar al'umma,su gagari iyayensu,harma kaji d'a ya dauki abun kaifi ya kashe mahaifi ko mahaifiyarsa ko 'yan uwansa,da yawa wadannan kurakuren dake cikin idda ko saki suke jawo hakan". "Tabbas......ko shakka babu" Sultane ya fadi yana jin wata irin gamsuwa da dukka bayanan haisam,yana jin wata cikakkiyar nutsuwa dashi. Kalar burikan da kowanne uba kanji akan haisam yaji ya saukar masa. Sai yakejin inama ace d'ansa ne?,inama ace mallakinsa ne?. "Koda bai zama d'anka ba,zai iya zama mafi kusanci sosai da kai......kana buqatar irinsa,sosai kana buqata" Ya gayawa kansa da kansa. Ya sani mulki abune dake buqatar mashawarta na qwarai,aqilan mutane masu nisan zangon hankali da fahimta,tsayayyu masu tsoron Allah. Yanaji a jikinsa kamar Allah ya aiko haisam ne cikin rayuwarsa,haka kawai yakejin wannan feeling din da baisan dalilin jinsanba,baisan kuma daga ina ya taso ba. Sanda lokacin sallah ya cika tuni masallacin ya soma samun dafifi na al'ummar agadez,masallata da suke halarta sallah a masallacin duk wunin juma'a,tun daga sallar asuba har isha'i,wanda daga nan sai kuma wani satin za'a sake budewa da bada daman shiga cikinsa,wannan ya sanya da yawansu a dukka wunin juma'ar a masallacin suke duka sallolinsu. "Bismillah" Sultane dake gefe ya fada yana nunawa haisam shimfidar da aka tanada saboda liman. Kansa ya saukar qasa,ba kasafai ya fiya son a bashi limanci ba daga zuwansa guri,saboda kaucewa fitina da susa cikin zukatan al'ummar gurin dama wanda yake da ikon jan sallar "Shiga mana ya sheikh......bismillah,umarnin sultane ne" Limamin da shike da haqqin jagoranta ya fadi fuskarsa dauke da murmushi. A nutse ya wuce gaba,ya kuma tsaya yana daidaita tsaiwar tasa,ya miqan hannu ya dauko qaramin mic din yana maqalashi gaban rigarsa,kafin ya furta. "Sawwu sufufakum(ku daidaita sawunku)" Muryar tasa ta bada amsa kuwwa daga kowanne nahiya na unguwar gaba daya saboda qarfi da nisan amsa kuwwar,yayi kabbara da husky voice dinsa cikin cikakkiyar nutsuwa. Sautin kabbarar daya isa har cikin kunnuwan akhnan dake tsaye tsakiyar dakin nata. Sautin ya bata wani irin baqon yanayin da batasan meye shi ba. Karon farko da kabbarar sallah daga masallacin ya taba fusgar hankalinta,har kuma takejin kamar baquwar murya ce wannan din. Kafin tace komai taji buhaina qasa qasa na cewa da birra,birran dake qoqarin gyara zip din zubabbiyar doguwar rigar da akhnan din ta sanya. "An nada sabon limanne ko sabon malami?". Kai birra ta girgiza "Banaji gaskiya,amma nima baquwar murya nakeji". A nutse akhnan ta daga kanta daga sunkuyar dashi da tayi saboda taje mata doguwar sumar da bushira keyi. " Aikin kula da lamuran da suka shafi masallaci dama aka baku?" Akhnan ta furta maganar da alamun bacin rai sosai cikin muryarta. "Tuba muke ranki ya dade" Buhaina tayi saurin furtawa. Batace komai ba,kaman yadda bata bada kanta bushira taci gaba da gyarawa ba,har kaman ba zatayi magana ba sannan tace. "Ya zama na farko kuma na qarshe da kunnuwaku zasu dinga damuwa da rayuwar wasu,harma ya zame muku abun tattaunawa.....wannandin dokata ce" "Bazai sake faruwa ba,ki mana afuwa" Birra ta fadi cikin duqar dakai. Siririn tsaki taja sannan ta maida kanta yadda yake tana fadin. "Banason wani dogon fi'ili,ribbon daya zaki saka ki hademin shi yadda bazai dameni ba" "An gama,in sha Allah" Bushira ta fadi tana ajiye kayan adon data debo a gefe. Shuru dakin ya dauka,kafin qarar wayarta ta katse shurun. A ladabce barra'u ta dauko wayar takai qasa saman gwiwarta tana miqa mata. Sunan kawai ta kalla ba tare da ta taba koda wayar ba. Shehnaz ce,sai ta bawa barra'u umarnin daga kiran ta saka a handfree ta riqe mata da hannunta. Hakan akayi,barra'u ta dora ma akhnan wayar saman tafukan hannuwanta,ta kuma matsa mata dasu daidai yadda zataji dukka abinda shehnaz zata fada. "Saluuut ma sœur(hello sister)" Ta fada cikin nuna kulawa da kuma yanayin sabo dake tsakaninsu. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 45 "Salut toi shehnaz....." Ta fada da nutsatsiyar muryarta dake sirkin qasaita a ciki,kai ba zakace can cikin qasan zuciyarta zallar tashin hankali bane. "Zuwa dare muna agadez in sha Allah,hankalinmu ya kasa kwanciya......fatan dai ba wani abu mara kyau ko?". Idanunta fa lumshe,tana kuma qoqarin zuqar numfashi,don so take ta daidaita kanta,ta kuma rage zafin da zuciyarta take mata. "Akwai matsala shehnaz......amma kafin kuzo ya zama tarihi.....zai shafe tarihin nasa ma gaba daya". Shuru shehnaz tayi tana juya maganar akhnan,idan tace akwai matsala eh tabbas akwai matsalar........ Sau tari tana da wani irin qarfin zuciya da ya gauraya da kafiyarta da yake sanyawa take iya tunkarar matsala komai girmanta,bata da shakka kuma bata da saurin tsoro. Ba komai ne yake girgizata ba,ba komai bane yake daga mata hankali ba. Matsala indai ba daga sultane ko mammina ba,basa taba gigita nutsuwa ko tunaninta,shi yasa a yanzun dukka rauninta ya nuna kansa,saboda sultane ne.....daga gareshi abun yake. Kafin shehnaz ta sake cewa komai akhnan ta bada umarnin gimtse wayar,ta dauke idanunta tana maidawa ga madubin dake ajiye a gabanta tana duban fuskarta. A nutse take duban yanayinta,taci alwashi ko waye wannan daya nemi gigita duniyarta saita shayar dashi mamaki,saita nuna masa illa da kuskuren abinda ya aikata din,ba zata taba qyleshi ba cikin kawo mata tsaiko da yayi na kwanakin nan a dukka al'amuranta,ba zata daga masa qafa ba......yadda ya kawo sabani tsakaninta da sultane,abinda ta jima rabon da ya faru a tsakaninta dashi. Kira na biyu ne ya sake shigowa,a nata zaton shehnaz ce still. A yanzu kam bata da wani juriyar sauraren dogon zance daga shehnaz din ko aisa ma gaba daya,inda zata qyaleta to tabbas zasu iso ne a daidai sanda shirinta zai kammala,maganar ma sai yafi dadi,amma kuma ga tarin mamakinta sai buhaina tace mata "Nannie ce". Manyan blue eyes dinta tadan bude kadan. Ba kasafai Nannie ke kiranta haka kai tsaye ba. A wasu lokutan dabi'unta suna kamanceceniya dana morsa safiyya,wani lokacin kuma tana diban kamannin halayyar mammina. Kai ya juya a hankalin dake alamtawa buhaina cewa ta daga kiran,ta daga din,ta sake dawowa ta duqa cikin girmamawa da wayar a hannunta. "Assalamu alaikum" Nannie ta fadi da kamilar muryar dinnan da yanayin jinyar da take ciki bai gaurayata ba. "Wa'alaikumussalam......Bonsoir nanniee(barka da yamma nannie)". " Bonsoir,comment allez-vous?(barka da yamma,kina lafiya?)" "Alhmdlh" Ta fadi tana hadiye wani abu a wuyanta. "Munyi magana da bappinki.....ya gayamin kina da baqo yau ma kaman yadda aka saba ko?" Tayi maganar da sautin da shi kadai ya fadarwa da akhnan gaba. Shuru ta yiwa Nannie din bata amsa mata ba,hakan kuma bai hana Nannie magana ba. "Biftu....." "Na'am Nannie" Ta amsata tana qoqarin tattala qwarin gwiwarta. "Yana da kyau ki dakatar da wannan wasan kwaikwayon haka nan.....lokaci yayi,muna da buqatar kawar daku daga gabanmu". Lumshe idanunta tayi sosai kaman ba zata bude ba,wani bacin rai ne yake taso mata. "Bana buqatar haka Nannie silvous plaît.......bana buqatar wannan hadakar.....zan iya rayuwata ni kadai na,hadin baya burgeni,rayuwar bata burgeni itama" Ta fada a sanyaye duk da akwai zafi me nauyi cikin kalamanta. "Biftu!" Ta kirata tana tsaurara kiran wannan karan. "Aure dole ne wuyan kowacce mace.....komai qasaitarki baki cika ba saida aure.......kina da zabi guda biyu.....wannan sune adalci na qarshe da zamu iyayi miki" Nannie ta fadi cikin nata zafin da akhnan din ta jima bata jita cikinsa ba. Wuta tsaf akhnan din ta dauke kafin ta janye jikinta daga kusa da wayar,sannan ta sulale ta zauna gefan gadon tana qoqarin gaya musu su fita a dakin su bata guri. Dukkaninsu sun fahimta,don hatta da buhaina da wayar ke a hannunta,wayar da tana iya jiyo Nannie na maimaita fadin. "Hello......hello" Haka ta fice da ita a hannunta. Bata da ikon katse kiran Nannie,don aikata hakan babban laifi ne,dole ta ajiye wayar a gefe har Nannie din ta gaji ta gimtse kiran da kanta. Ta gama fahimta ta kuma gama gane komai,wannan karon al'amarin yafi kama da taron dangi akayi mata,momma......Nannie uwa uba sultane dinma. Zata tsammaci hakan daga momma,harma sama da hakan,amma daga sultane kuma ko Nannie dukka baqon abu ne a wajenta. Wai wanne dalili ne zai sanya ba zata tsani morsa safiyya ba?.......me yasa ba zataji bata qaunarta ba?. Tana da cikkakken imani da yaqinin komai ita ta assasashi,komai kuma ita ta shiryashi,in fact ma jikinta yana bata ita ta jawo komai ta hadashi daidai da muradinta da cikar burinta. Tsam ta miqe tana zare ribbon din kanta,ta kuma daure gashinta tsakiyar kanta da wani irin zafi,jelar ta sauka gadon bayanta tana lilo. Banda umarnin daga sultane ya fito......bata tunanin yau duk duniya akwai wani wanda ya isa ya sanyata ta fuskanci wannan baqon. Umarnin sultane ne......zata cikashi,amma kuma ta hanyar da takeso,ta kuma hanyar da taga dama itama. *FALAAK* Sallamar morsa safiyya ya sanyata daga kanta daga duba shafin littafin dake hannunta,wanda kusan ta zauna ne kawai tana duba littafin saboda ragewa kanta lokaci da kuma dogon zama,amma sam ba wai don tana jin dadin karatun bane. "Ya dai?" Morsa ta tambayeta tana zama daga gefe hadi da qoqarin gyara lullubin tattausan mayafin jikinta. Ajiyar zuciya falaak din ta sauke tana rufe littafin. "Gaba daya momma ji nake kaman karatun ya fita a kaina,oustaz Ousmane ya iya karatu morsa,gani nake kaman ba zamu samu wanda ya kaishi ba". Murmushi kadan momma ta saki tana daukan remote don sauya channel din dake aiki zuwa TRT africa. "Ba'a gaggawar yanke hukunci,kuma kowanne dan adam da irin baiwarsa,sani ne bamuyi ba". Kai ta gyada a hankali falaak din,momma taci gaba da cewa. "Ya iso tun tuni,suna masallaci da sultane,bayan sallar la'asar din zai shigo,kuma naji ma an idar da sallar.......ki yiwa baraka magana ta hada miki kansu Aafreen ku wuce gurin daukan karatun,kar a fara saba dokarsa tun a ranar farko". Numfashi falaak taja tana tabe baki. Wannan malamin me tarin doka da tsarin tsiya zataso ta ganshi,zataso ta gani ta kuma san irin ilimin da yake dashi haka da har ya zarta oustaz Ousmane yake sanya dokokin da ko shi bai taba sanya musu su haka ba. *SULTANE* Yadda haisam ya saba zama yayi musabaha da mutanen dake bayansa bayan kammala salla a masallacin juma'a na jimma,haka ma yanzun yayi. Abun da ya baiwa mutane da dama.mamaki aka shiga kallon kallo ganin yadda ya baiwa sultane hannu kansa tsaye. Irin wannan kwarjinin da yake musu kaman sam shi bai masa ba?. Qasan ran sultane yake murmushi,wani irin nutsuwa na shigarsa tattare da haisam din. A cikin ayyukansa da dukka motsinsa ya fahimci yadda ilimin addini ya wadaceshi qwarai da gaske. "Ayi masa tattaki zuwa,sannan a sake inganta gurin karatunsu idan yanayin da aka tanadarwa gurin bai masa ba" Umarnin da sultane ya bayar kenan. Cikin girmamawa haisam ya rusuna,da hausarsa da bata bada miqaqqen sauti da amo irin na cikakken bahaushe ba yace. "Godiya nake". Duk wani taku nasa yana tafiya ne da ilimi ankarewa da kuma karantar kowanne motsi na gidan. Kowanne taku da zaiyi yana yinsa ne cikin sanyawa abubuwa da yawa alama.......haddace yanayin abubuwa da kuma gilmawar kowanne mutum da motsin iskar dake kaiwa tana kawowa. Kafin su isa gurin ya gama rarrabe tsarin sassannin da ainihin kebantacciyar daular da iyalin sultane ke ciki,adadin sassan ya kuma fahimci sassan matan nasa......banbancin hadimai na kowanne sashe,duk da bai gama tabbatar da hadiman sassan mammina da na momma ba. Basu gama shiga gurin ba,amma tun daga farko yaji gurin yayi masa,tun daga farkon gurin kuma yasan gurin kebantaccen guri ne na musamman koda kuwa a cikin gidan. Kai tsaye zaka iya kiransa da gandun daji,saboda yadda aka qawata gurin da nau'ikan shuke shuke 'yan qasar France. Akwai wata qirqirarriyar qorama me wasu fararen duwatsu da kifaye masu nau'ika daban daban dake kai.kawo a ciki. Ido ya lumshe ya shaqi iskar gurin a sirrance. Saita tuna masa da nasa sassan daya ajiye musamman a jimma,wanda yake da kwatankwacin wanna tsarin gaba dayansa. A duk sanda yakeson duba wani babban littafi,yin research akan wata mas'ala,ko kuma yin research game da wani security issue daya shafi security intelligence yafi zama a nan,zai kammala komai a nutse yana kewaye da hadimai,don a irin wannan lokacin nanay kawai yake bawa izinin ganinsa,sai kuma mooti,wanda yawa yawan lokuta yafi zuwa ya sameshi a gurin hutawarsa dake cikin gidan,ko cikin fadarsa idan buqatar ganin ta canne. Kanta na sunkuye tana ta qoqarin sake duba karatuttukan baya,yayin da har yanzu zuciyarta keta kai kawo,ta kuma kasa jin wani cikakken aminci da malamin. Alamun takun da taji shi ya sakata daga kanta tana tsammanin ko su aeera ne suka tashi daga gurin da zasu dinga nasu karatun da yake gefanta kadan. Karon farko idanunta ya sauka a kansu. Mutum uku ne......da guda biyu kawai ta sani a cikinsu. Maher daya kasance kaman dalibin oustaz Ousmane,sannan kuma jifa jifa takan ganshi tsakanin sassansu duk da batasan me yake zuwa yi ba. Na biyun bala ne......daya daga cikin manyan hadimansu,sai na ukun...... Mutum na ukun daya banbanta da kowa a cikinsu,mutum na ukun da ta ganshi ya fita daban,tamkar gold din da aka jefa tsakiyar gama garin qarafa. Cikin nutsuwa yake maganar da bata iya jin me yake fada,amma dai ya janye rawaninsa zuwa qasar habarsa,abinda ya bawa kyawawan labbansa masu sulbi damar fitowa,suna kuma juyawa a hankali. "Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Ta furta da sauri da qaramin sauti tana janye idanunta gefe daya saboda wani mummunar faduwa da gabanta yayi zuciyarta na qara wani irin mahaukacin bugu da bata taba jin haka a tattare da ita ba sai yanzu. Cikin jikinta takejin qarin kusantowarsu da gurin,yayin da bugun zuciyarta har yanzu yaqi daidaituwa,wasi wasi kuma ya cika mata zuciya tanason rarrabe waye malamin a cikinsu?. Bala dai ta sanshi,saboda haka ba wata magana a kanshi,Maher kam bata tunanun oustaz Ousmane zai kawo Maher a mazaunin malaminsu bayan dalibi ne shi kansa a wajensa. Sai kuma na ukun?....... Sam bai mata kama da malamin da zai shiga gidan sarauta da zummar koyarwa ba. Ta kowacce fuska kamanni dama yanayinsa. Wani irin kwantaccen kwarjini take gani yana haska kowanni motsi nasa,irin kwarjinin da a fuskar sultane kawai take ganinsa. Eh akwai kamala me yawa da wata irin nutsuwa shimfide saman fuskarsa......yanayin shigarsa ya sake tabbatar mata da yawan ilimin daya ratsa halittarsa gaba daya,to amma......" "Sheik haisam ya iso ranki ya dade....." Muryar bala daya tsugunna saman qafafunta ta dauko hankalinta zuwa wajen. "SHEIK HAISAM" Ta maimaita sunan tana motsa labbanta,tana kuma jin wani irin sanyi da taushi a iya sunan kawai. "Eh gashi can Allah ya taimakeki......sultane yace a gaya miki,a bashi dukkan girmamawar da shi zaa bashi,a yanzun sheik malaminsa ne". Kai take jinjinawa a hankali tana jin kanta kaman ya mata nauyi,bugun da zuciyarta kuma keyi yana nan bai sauya ba. Da iya saqon sultane kadai tana iya fahimtar muhimmancin da ya bawa abu "Na barku lafiya" Bala ya fada yana tashi gami da juyawa suna barin gurin shida Maher. Shurun da taji sai muryar Aafreen kadan take tashi ya sanyata waiwayawa kaman me ciwon wuya. Fuskarsa shine abu na farko data soma sauke idanunta a kai. Wasu irin zagayayyun idanuwa masu girman da suka bayyana kansu tsakanin fuskarsa data zama circle cikin rawaninsa. Yana zaune sosai saman babban kilishin dake shimfide a wajen ba tare daya damu ya zauna kan kujerun da aka ajjiye masa ba a wajen masu tsananin taushi. Aeera ce zaune a gabansa,ta bude littafinta na nuraniyya,ya dora yatsansa akai itama haka,da alama karanto masa takeyi,sai Aafreen dake zaune daga bayan aaera kadan,ta tallafe habarta da hannunta tana kallonsu fuskarta yalwace da fara'a,da alama akwai abinda yayi mata dadi. Sake janye idanunta tayi tana kiran sunan Allah. Sai take jinta gaba daya kamar a rude take,kaman ta fita daga nutsuwarta ta dazu. Canki canki takeyi,ita zata kai kanta?,ko kuma idan ya gama da yaran zai nemeta?. To amma tunda suka shigo gurin bataga wani alama da zai nuna yasan da wanzuwarta a gurin ba,baiyi wani motsi ko yaya da zai alamta mata yasan tana gurin ba. Bata da wani karsashi ko qwarin gwiwa,don haka ta zabi ci gaba da zama a gurin,ta sunkuyar da kanta kan littafin,duk da bata gane komai,bata kuma fahimtar komai,kacokam hankalinta yana wajensu da bata iya jin tasa muryar,sai muryar yaran kawai,su dinma yau cikin nutsuwa suke magana. Jifa jifa tana satar kallo su,saidai ko sau daya ba wani alama daya nuna ansan da zamanta a wajen. Ta sauke ajiyar zuciya daidai sanda taji muryar aeera saman kanta. "Kizo inji sheikh haisaaam". Yadda yarinyar ta furta sunan da wani irin tone sai taji sunan ya sakeyi mata dadi,ya kuma qayatar da ita dari bisa dari,qasan zuciyarta da dan mamakinsa na yadda ya aika tazo din ta tattare litattafanta ta miqe tana sake satar kallonsa. Tanason ta banbance yaushe ya kalleta har ya fahimci tana gurin ma?,saidai kuma har ta isa gurin ta tube takalmanta ta zauna a nutse bata gane komai ba. "Wa'alaikumussalam warahmatullah" Ya furta Kansa yana saman littafin Aafreen da oustaz Ousmane yake basu aiki lokaci lokaci. Qara tsanantuwa bugun zuciyarta yayi,har ta gaza yin qasa da kanta ta daga kanta tana dubansa kai tsaye. Abubuwa biyu suka rikitata,na farko wani baiwa dake cikin sautinsa da muryarsa da bata taba jin irinsa ba,na biyu kuma tasan yana son gaya mata batayi sallama ba. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 46 __________________________ HALY JASHERU VENTURES. munada tsuntsaye na kasashen waje masu kyau da daukar hankali kmn haka. TATTABARU French modain(Argentina) Indian faintail (3in1) indigo,opal,Andalu,Lahore,busa,Bukhara, indomie,Jacobin dasauransu. KAJI. Brahma,silkie,silver lace,coshine,dawisu, parrot (aku)dasauransu. , Munada kayan Islamic center.habbatus saudah,hulba,zaitun,qusdul Hindi,minannas,Rose water dasauransu,dangin garinsu ,mansu yayansu ,ganyensu. munada original Zuma,yar chad da mombila. Munada kayan gwanjo masu kyau daga jariri zuwa babba, Overall,Rumpers, bodysuit, sweaters,wanduna, tracksuit dasauransu,munada kaya masu kyau na bacchi na gwanjo. Munada Ethiopian magic hair oil 🪔 Wanda yake Kara gashi,yayi tsaho laushi,yayi Baki drct daga Ethiopian muke kaisa ko Ina afadiin duniya. Don Neman Karin bayani number waya 07046665338. ___________________________ Ba dabi'arta bace rashin yin sallama idan ta riski guri,sosai aunt hairaan ta dabi'antar dasu da wannan dabi'ar. Su din rainon hairaan ne,hairan kuma rainon morsa safiyya ne,don haka sun samu ladabi da kuma horaswa wajen qanqan da kai me yawan gaske. Miqewa tayi,tayi taku uku ta sake dawowa sannan tayi sallamar. "Assalamu alaikum warahmatullah". A nutse ya daga idanunsa,yayi mata kallo daya sannan ya maida kansa yana amsa mata,kallo guda dayan daya tilasta mata sulalewa ta zauna saboda rauni da jikinta taji yayi mata. Ya danji mamaki kadan qasan ransa,bai tsammaci haka da sauri ba......amma sai ya tuna da wasu daga bayanan Maher. Zata iya cewa bata taba ganin kyawawan idanu irin nasa ba,wasu irin idanuwa masu wani irin kwarjini a cikinsu. "Bata litattafan da kukeyi mu gani" Ya fada yana nuna aeera. Duka ta miqawa aeera litattafan,ta kawo gabansa ta ajjiye,ya saka hannunsa a nutse ya daukesu ya soma dubawa bangon daya bayan daya. Sanda ya kammala sai ya gyara zamansa. Tambayoyi ya fara jefa mata,a nutse yake mata tambayar,bai kuma tsaurara da yawa ba,amma duk da haka a rikice take jinta,abinda ya sanya wasu tambayoyin ta amsasu da qyar,wasu kuma ta kasa amsa su din saboda da gaske bata sansu ba. Shuru yayi bayan ya gama tambayoyin,yana dan danna wayarsa a hankali,yana ganin kimar macen me tarin ilimi sosai......hakan kuma yana burgeshi,wannan ne ya zaba sila kuma dalilin da bai bar su rumaisa sarauta ta sakasu sun zama daban da mutane a duniyar ilimin addini ba. Ya sake qarfafa hakan akan noory ita dake tasowa yanzun. Duk da yayi qoqari......amma akwai tambayoyin da yake ganin ya kamata ta amsa su compulsory. Sam ba wadannan litattafan ya kamata ta fara dasu ba,har cikin ransa yaji ya aminta zasuyi karatu na gaske da yaran,bawai karatun da bincike ne ya shigo dashi ba. Yadan dauki sakanni kafin ya motsa labbansa. "Wadannan litattafan za'a canzasu da wasu" "To" Ta fada tana gyada kanta. Haka kawai tun daga gabar farko takejin wani sauyi a tattare da ita. "Hizb nawa kike dashi a qur'ani?" Ya sake tambayarta yana ajiye wayarsa a gefe a gefe hadi da karbar aikin gwajin daya bawa Aafreen ta kuma kammala. "Ashirin da biyar" Ta samu kanta da amsawa haka kawai tana jin nauyi. Bai sake cewa komai ba yaci gaba da duba aikin Aafreen,yana mata bayani a nutse a guraren da tayi kusakurai. *_AKHNAN_* Tanajin ne kaman bata da wani cikakken qwari a jikinta,tana jin kamar iska ce ke sarrafata ba qafafunta ba. Ita kanta iskar kaman tasan a yanayin da take,kamar tasan me takeji taci gaba da kadawa a hankali tana watsa sassanyan qamshin turaren jikinta zuwa kowanne sassa na gurin. Buhaina da birra na daga bayanta suna kula da inda take dagawa da sauke qafarta. Daga bayansu kuma yalwa ce,tana biye dasu ne bisa umarnin mammina,ta turowa akhnan ita ne kawai,ita ma bata ce komai ba tunda tasan wace yalwa?,wanne matsayi take dashi a gurin mammina. Tasa a ranta mammina tayi hakanne kawai don ta sake bata tsaro kulawa da kuma damar sakewa. A kowacce hanya da zata sadata da inda ta saba ganin baqin nata.......masu tsaro ne data tabbatar ba na masarautar agadez bane,sunfi kama da masu tsaron lafiyar 'yan siyasa ko kuma masu kudin da suka ci suka tayar da kansu. Dukkaninsu cikin baqaqen suit suke da baqin gilashi da suka manne fuskokinsu dashi. Wasu daga cikinsu akwai bindiga rataye a qugunsu. Ba iya gurin ba kawai,ta fahimci masarautar ma gaba daya kamar an sake qara tsaronta sosai. Qaramin tsaki taja,ba wani abu guda daya burgeta tun daga nan. Ba jama'ar da suke debowa suzo dasu ba......har yanzu bata tunanin akwai wanda zai taba fahimtarta,akwai wanda zai iya karanta mind dinta ya fahimci komai. Lallausan gurin ma'abocin shuke shuke da akayi linking nasa da sabuwar RAUDHA inda zai zamana gurin zaman karatun su falaak kamar yadda morsa safiyya ta bashi suna. Daga kowanne taku irin wadancan mutanen ne data gani daga hanya suna qame. Kusan dukkaninsu sama suka kalla ballantana kayi tunanin hankalinsu yana kanka. Daga can nesa kadan take iya hangen mutumin da dukka jikinta da zatonta yake bata tabbacin shine baqon nata. Matashin saurayi ne,fari sol dashi,me wani irin haske da yake bata tabbacin BUZU ne d'an qabilarsu,ko kuma wanda yake da alaqa ta asalin mutanen Istanbul na daular turkiyya. Kaman ragowar mutanensa,sanye yake shima da baqaqen kayan da suka mugun shan banban da na jikin mutanensa. Saboda shi din trouser ne da shirt a jikinsa da suke bayyana irin asalin tsadar da yadin da aka samar dashi yake dashi. A tsaye yake yadan bada baya yana amsa waya,hannunsa daya soke a aljihun wandonsa yana dan tattakawa daga hagunsa ya koma dama. Idanunta taja ta lumshe tana jin wani baqinciki yana kamata. Ko na qiftawar idanu......koda na qaramin taqi bata ga wani dacewa ko hadi ba ko guda tsakaninta da shi ba. Bata ma hangi wani kamala a tare dashi ba......baiyi zubi ko komanceceniya da mutanen da sukasan meye ma'anar class ba a cikin dabi'unsa da halayensa ba. "Wow" Kalmar ta sauka a kunnenta sanda take dab da isa gurin,lokacin da bacin ranta yake sake ninkuwa a duk sanda take qara taku zuwa gabansa. Manyan blue eyes dinta ta daga tana dubansa,wani irin kallo yake qare mata daga samanta har qasanta,fuskarsa shimfide da wadataccen murmushin dake nuna zallar maqurar burgeshi da tayi. Duk kuwa da cewa baya iya ganin komai tattare da ita banda kyakkyawar fuskarta. Baya iya ganin komai nata sai zara zara yatsun hannunta data sanya ta dafe bayan kujerar data ja tunga kusa da ita tana kasa qarasowa. Wani irin abu ne yaji yana mamayarsa me girman gaske dangane da ita. Iya tsahon rayuwarsa,idanunsu basu taba sauka akan wata mace da yaji ta burgeshi haka irinta ba. Bai taba sauka akan wata mace da yaji ta sauke dukkan alfaharinsa ba sai a kanta. Ya lumshe idanunsa kana ya budesu yana imagination dinta a mazaunin matarsa. Tabbas zai zarce sa'a,zai kuma sake zama na daban. Tun daga samun damar ganawa da ita a karon farko ma ba abu bane me sauqi,long process ne da baisan watanni nawa daddynsa ya dauka ba kafin ya samar masa izinin. An gaya masa,ya kuma ga alama......da gaske tana da izza,tana da qasaita,akwai jinin sarauta sosai tattare da ita,ya gani kuma a yanzun. Tsaiwarta kawai wani abu ne me burgewa a idanunshi,sai ya kasa riqe kansa,ya kuma kasa controlling kansa,ya kasa jiranta har sai ta qaraso,duk da warning dinsa da yayarsa tayi. "Irinsu basason a fiya zaqe musu......irinsu suna son namiji ne me izza irin tasu ko kuma wadda tafi tasu.....ka kame kanka ramadan......karkayi saurin bada kanka.....duk da na sanka,kana da irin aji da quality din da kowacce mace ke so,amma muddin kaci nasarar sato zuciyar the princess of agadez kingdom.......to mun sake samun qarin wata martabar ne da daraja,koda a cikin family zamu sake daukakuwa fiye da daukakar da muke da ita a yanzu". Tazarar da ya bari a tsakaninsu bata da yawa,ya tsaya qyam a gabanta yana ci gaba da kallonta. Yana jin kansa kamar zai narke a gaban nata,dukkan wani surori na kyau,dukkan wani hasashe da yakeyi ashe nisa dake tsakaninsu ya rage komai?. Wata irin ingantacciyar fata ce da ita dake tarwai kaman zaka hangi komai dake yawo tsakanin bargo da tsokar jikinta,kamar batasan wani abu da ake kira da qura ba sam sam. Kyawawan idanunta da ba Kasafai aka fiya samunsu a nan ba......sunfi yawa tsakanin mutanen Asia da sauran qasashe. Cikakkiyar girarta da kuma gashin idanunta zara zara da suka qarawa fuskarta kyau da kwarjini. Cikin mintunan da basu haura biyar ba taji wani irin bacin rai yana saukar mata. Ta tsani yawan kallo,ta kuma tsanu kallon qurilla,koda daga gurin 'yar uwarta mace ne ballantana a jinsin maza. Zaro hannunsa yayi daga aljihun wandon nasa,yana jifanta da wani irin murmushi da yasan yana da matuqar tasiri gurin 'yammata da yawa,ya miqa mata hannun yana fadin. "Sunana Aabood ramadan farree,ni d'ane ga ambassador ramadan farree,duk da nasan zaki sani,mahaifina sanannen mutum ne ba boyayye ba,babban mutum ne a qasar nan.........zamu iya......". Lallausan hannunta da babu d'igon komai ta daga masa tana duban tsakiyar idanunsa. Cikin muryar nan tata dake cike da izza ts soma magana. "Ba filin sanin salsala da nasaba mukazo ba......a taqaitattun jimloli bakayimin ba......" Ta qarashe maganar tana juyawa don barin gurin. Da hanzari ya tako ya kuma sha gabanta yana qoqarin controlling tashin hankalin da yaji ya shiga. "Ya da sauri haka?......ya kuma da gaggawar yanke hukunci haka?,ai kamar ya kamata ki bamu dama da lokaci koda mintuna biyar ne mu gama sanin juna". Wani irin kallo ta daga idanunta ta watsa masa. Qasan ranta takeji eh lallai.......sultane yana dab da sarayar mata da daraja mutunci da dukka kimarta,wannan ruhin me dimbin daraja da tsada sultane na dab da maidashi wani abu maras kima ko qanqani. "Mintuna biyar?,ka kuwa san da waye kake magana har kake neman mintuna biyar daga cikin tsadaddun lokutanta?,banda darajar sultane kana tsammanin har ka mutu kana da darajar ganin fuskar akhnan muhammad hammud ne?". Ta qarasa maganar tana jin ranta yana sake dugunzuma. Sak yayi yana kallonta,yana jinjina izzarta. Kalar izzar da tasa ya raina dukkan wata izza tasa da ake batun yana da ita. Kalar izzar data sanya yaji ya soma dulmiya a kogin sonta,tako ina yana jin tayi masa. "Amma dai da zaki daure ayimin wannan alfarmar......beside ma bansan me zance da daddy ba a kanki......" "Ka fadi mishi dukkan abinda kaso wannna matsalarka ne.......amma dai karka canza daga abinda akhnan ke akai yanxu......akhnan ba matarka bace.....don bakayi mata ba" Ta fadi tana ci gaba da taku zata gotashi. Bisa tsautsayi ya miqa hannu don dakatar da ita,ganin kalaman baki basu isa su dakatar da ita ba,yayi nasarar riqo gefen mayafinta yana fadin. "Silvouse plaît" Cak ta dakata,qirjinta yana wani irin luguden duka. A tsahon tarihin rayuwarta,idan ka cire sultane......babu wani d'a namiji guda daya da taba samun damar kama koda zaren da aka dinka tufafinta dashi,bare ya riqe mayafin dake yane a jikinta. Baisan girman kuskuren da ya tafka ba,shi ya sanya yaci gaba da tsara mata kalaman da yake ganin zaisa ta fuskanceshi. Tsakanin buhaina birra da yalwa basusan waye yafi wani gigita ba da ganin irin kalar kuskuren da abood ramadan ya tafka ba,saidai dukkaninsu basu kai ga tantance abinda zai iya faruwa ba qarar saukar marin ya isa ga kunnuwan mutane da dama......cikinsu kuwa harda haisam da falaak wadda ta gaza motsi tun sanda akhnan ta fara magana da abood. Tun shigowar akhnan din tajishi saboda gurin daya ne,wasu tsararrun shukoko ne masu tsaho da kauri kawai suka banbamta gurin. Cikin wani irin razana da tashin hankali falaak ta daga idanunta ta can qasa tana satar kallonsa sanda yake ci gaba da sauraron karatun Aafreen. Ba wani yanayi dake fuskarsa daya canza. Bataga alamun ma yaji komai ba,abinda ya sanyata a dimbin dimauta da kuma kokwanto. Babu ta yadda za'ayi yace baiji abinda ya faru ba,tun daga shigowar biftu gurin baqinta har kawo yanzu ba. Tayi imanin koda kana nesa da inda su suke karatun xaka ji komai ballanta a nan din inda suke zaune koda takun sauke qafafu saman ganyayyakin da suke zube a qasa kana iya jinsa. To amma me yasa yayi kamar baiji ba?,me yasa yanayinsa ya nuna baiji komai ba?. Qanqame hannuwanta da idanunta tayi sanda kalaman akhnan na qarshe cikin tsananin fushi suke fita. "Idan kai mahaukaci ne ya kamata kasan guraren da zaka dinga gwada haukarka.........in bakayi wasa ba tabbas ba zaka fita daga masarautar agadez da qafafunka ba,zan ganar dakai kuskurenka.......ka gaggauta kwashe karnukanka ku fice mana a masarauta,domin nan din ba bariki bace" "Me yasa yaa biftu?......me yasa?" Falaak ta fada can qasa tana jin jikinta yana daukan rawa. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 47 __________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah ____________________________ Ba ita aka mara ba amma tana jin saukar sautin marin har yanxu,tana jin takun akhnan da yalwa ke faman sanyayawa rai "Allah ya huci zuciyarki shelelen sultane,.......Allah shi baki haquri......ya tafka kuskuren nan ne duk a rashin sanin wacece ke......ayi masa afuwa da gafara" Har taji takun nasu ya mata nisa alamun sun fice a wajen. Da qyar ya iya riqe numfashinsa zuwa sanda Aafreen takai qarshen surar. Ya maida bangon qur'anin ya rufe yana qoqarin controlling hannunsa ya furta. "Ma sha Allah" Yana miqa mata qur'anin. "Yaaa falaak" Ta tsinci muryar Aafreen tana kiran sunanta,abinda ya dawo da ita hayyacinta kenan. Ta daga kanta da sauri sai suka hada idanu,ba shiri ta maida kanta qasa. Kusan sakanni goma bai sake cewa komai ba,kafin a nutse yace. "Ki tabbatar kin ajiye komai daga bakin qofar nan kafin ki shigo aji,nafi buqatar koya karatu ga wanda yasan girman abinda nake koya masa din........na biyu jilbab,ki nema jilbab wadatattu da zaki dinga zuwa daukan karatu dashi......na uku....." Sai yadan dakata kadan yana daidaita numfashinsa. "Ki nemi wadda zaku dinga zuwa karatu tare da ita,bazai yi ajinki ya zama ke daya bace" Ya fadi yana jin komai dole ya zama bisa tsari na shari'a. Baya taba yarda da batun kebewa koda wane muddin macace don kiyaye hukuncin Allah da haqqin addini. Kai ta jinjina a hankali tana sake yin qasa da kanta,mamaki kuma yana sake kasheta. Dan siririn murmushi ya saki yana miqawa Aeera me shekaru hudu hannu. "Ilallliqaaa" Ya furta da tataccen larabcinsa,sai yarinyar ta saki murmushi itama tana maida masa amsa. "Liqa'ana bi khair" Duk da qarancin shekarunta tana jin yana burgeta,tana jinsa kamar wani abbanta ko yayanta. "Yaa falaak.......an tashi fa" Aafreen ta fadi wadda ta miqawa ramma litattafanta ta tsugunna tana qoqarin sanya takalman qafarta. "Zan taho yanzu" Tace dasu tana miqawa ramma litattafanta. A girmame ta amsa,taja hannun yaran suna wucewa. Tsam ta miqe,ta zura lausasan takalmanta tana jin jikinta gaba daya ya sake,zuciyarta kuma tana cakuduwa da wani irin yanayi guda biyu. Takawa ta dinga yi a hankali,har ta zagaya ainihin masaukin baqin akhnan din. Wasai yake babu kowa,alamun an gama,kuma kowa ya kama gabansa. Da wani irin mutuwar jiki ta qarasa ta zauna saman daya daga cikin kujerun dake a wajen ta zauna. Wai meke damun yaa biftu ne?......mari?,marin ma a fuskar namiji me cikakken hankali da kuma shekaru?. Ta yaya har take da zarra da qarfin halin d'a namiji?. Yaushe zatayi aure?,yaushe zata fahimci aure yana zama wajibi akan mace irinta?,sai yaushe zata daina raina maza har haka?. Yadda qarar marin ya riskesu ya dawo mata,takai hannunta fuskarta tana shafawa. Me yasa yayi kamar baiji komai ba?,me yasa yayi kamar baiji abinda yake faruwa ba?. Ta tambayi kanta bugun zuciyarta na qara gudu da iya tunawar da tayi kadai da fuskar sa. "Saboda bai shafeshi ba,ba huruminsa bane" Wani sashe na zuciyarta ya bata amsa nakai tsaye,amsar data sanya murmushi subucewa daga fuskarta duk da ba a yanayin take ba. Wannan shine kalar saurayin da yake burgeta,wanda ba ruwansa da shishshigi.....kalar mutumin da sam baya shiga sabgar da ba tashi ba.....MISKILI NE kenan da gaske?" Ta yiwa kanta tambayar tana rungume hannayenta a qirji. Daga kanta tayi sama,duhu ya fara raguwa sosai,alamun dake nuna magariba tana dab da qarasowa,saita miqe a nutse tana sake harde hannayenta a qirji tana kuma takawa don ficewa a gurin. Saidai har yanzu murmushi yaqi barin saman fuskarta,tana ta jimami tanata kokwanton ba zasu samu kaman oustaz Ousmane ba........sai ga wani da yasha banban dashi ta kowacce fuska. Ba karatu yayi mata ba yau din,yau din ta cika ne kawai da tarin tambayoyi,amma yanayin tsarin da ya aza nasa karatun ya bata gamsuwar dari bisa dari shi na musamman ne. Amma ya cika izza da yawa,kaman akwai tasirin sarauta a jininsa,dukka motsinsa da yanayinsa ya mata kama da wani basarake ko masarauci,saidai ba wata qwaqwarar shaida daya nuna hakan,ta yaya karatun zai kasance?" Ajiyar zuciya ta saki nannauya tana kai tafukan hannuwanta ta shafi fuskarta. "A hankali falaak,wannan dogon tunanin duka na meye haka?" Ta tambayi kanta da kanta,tambayar data sakata sakin murmushin dole. "Tsarinsa ne da yanayinsa kawai yayimin" Ta bawa kanta da kanta amsa,batasan ko tayi daidai ba ko batayi ba,iya amsar da takejin zata iya fita daga zuciyarta kenan a daidai wannan lokacin. *AKHNAN* Ko sassan mammina batayi sha'awar komawa ba ta dakatar dasu yalwa tun daga farfajiyar data raba sassan sannna ta wuce sashenta. Tun a falukan farko ta dakatar da kowa,tace dukkan wani motsi bata sonshi,kowa yayi nesa da inda take ta wuce kai tsaye zuwa dakinta. Da kanta ta dinga zare kayan jikinta tana watsarwa,tana jin tsanar suturar tana mamayarta. Irin abinda take gudu sultane yake shirin jawo mata?,wannan din shine mutum na goma sha biyu cif da sultane ya tilasta haduwarta dashi,yanzu har yakai?,har yana da zarrar kama gefan mayafinta?. Kuka take so tayi,amma sai takejin bashi da martaba da darajar da zata zubda masa hawaye. Bashi da wannan alfarmar da hawaye zasu zuba a idanunta ta dalilinsa,kawai abu daya takeji......kaman ya kamata hukuncinsa yafi marin da tayi masa. Toilet ta shiga,ta sake wanka gaba daya,tana jin kamar ya samu nasarar taba jikinta ne ba mayafinta ba. Ta wanke jikinta sosai tana jin kamar ta sauya fatar jikinta,ta fito daure da towel fuskar nan cike da wani irin fushi. Ta jima zaune tana jira ruwan jikinta ya tsane da kansa,don ko samun damar gogeshi batayi ba,zuwa sannan kuma har ta jiyo kiraye kirayen sallar magariba,don haka ta miqe a kasalance ta shige closet dinta tana laluben kayan sawa,abinda bata saba bata ma iya ba,wannan ya sanyata kafin ta kammala ciro wani up and down skirt da blouse dinsa da dan madaidaicin scarfs dinsu taji ta gaji tubus. Gaban mirror ta tsaya tana kallon kanta,har yanzu zafin abun takeji har cikin fuskarta. Ba wanda zata nema,ba wanda zatayi magana dashi har sai sun nemeta da kansu. (08187255862 lu'u lu'u paying) Wani irin kyau kayan sukayi mata,sun fiddata kamar 'yar qasat turkiyya din,ta aza abayar sallarta a sama ta tayar da sallah. *MAMMINA* Tunda suka fita da yalwa tana zaune daga bakin babban window din da yafi kama da qofa,wanda ya bada wani irin yanayi me kyau da take iya hangen lambun dake liqe da sassanta. Wayarta na a hannunta tana duba fuskar wayar lokaci bayan lokaci,yayin da gabanta ke shaqe da nau'ikan kayan ciye ciye na kayan marmari. Idan tace hankalinta akan akhnan yafi rinjaye tayi qarya,a yau hankalinta na saman wayarta fiye da kan akhnan din. Takun da taji ya sanyata juyawa da wuri. Ayaana ce take takowa a nutse,ta yarda qwarai da hankalin ayaana,wanda wannan yarda da hankalin bawai ta sanya ayaana ta samu daman sanin komai daya shafeta bane. Ta tsaidata iya matsayinta na babbar jakadiyar dake da ruwa da tsaki akan dukkan al'amuran da suka shafi bangaren sassanin matan sarki. "Allah ya baki yawan rai" Ta fada tana rusunawa. "Tamim ne iso......nace bari na shaida miki kamar yadda kika buqaci hakan" Kai mammina ta girgiza,tana sauke qafafunta qasa. "Ki masa iso......yalwa kadai na yarda a sake bari ta qaraso nan". Jinjina kai ayaana tayi tana furta. " An gama" Can qasan ranta yana cika da mamakin irin wannan zuzzurfan kusancin da ba kowa ke iya karantoshi ba. Ita kanta ba zata tuna lokacin da tamim ya shigo gidan ba......ba zata iya tantance sanda ya fara wanzuwa a gidan ba......amma zuwa yanzu,mutane kadanne suka fishi daraja da kuma matsayi gami da kusanci da manyan gidan. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 48 ___________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah _____________________________ Kafin tamim ya shigo,sai ta dinga jin kamar lokacin yayi mata tsaho. Ta miqe tsaye,ta taka a hankali zuwa bakin qofar shigowa gurin tayi tsaye goye da hannayenta tana jiran qarasowarsa. Bata cika mintuna biyu ba cikakku tamim ya bayyana a gurin,da wannan suffar tasa dake nuna qarfi da lafiyar da yake da ita. Zubewa yayi a gabanta,kwatankwacin bawa da uban gidansa,kansa a maqasqancin qasa yake magana. "Barka da wannan lokaci,barkanki da warhaka uwar gijiyata". Sauke hannayenta tayi tana fesar da iska daga bakinta,ta kuma koma da baya ta zauna tana fadin. "Ba lokaci bane na gaisuwa yanzu.......lokaci ne na aiki,aiki kuma tuquru,lokaci ne na cimma muradai.......banaso lokaci ya quremin,banaso ya kasance komai ya kasance cikin qurataccen lokaci......har yanxu banji kalar labarin da nakeso ba" Ta qarshe maganar cikin girma tana zama saman daya daga cikin kujerun dake zagaye da gurin,ta ware tafukan hannayensa tana miqa masa. Murmushi ya fidda me sauti,sannan ya miqe tsaye. Babbar riga ce a jikinsa wadda aka fi sani da malum malum,wadda aka yiwa aikin hannu dake dauke da zanen tambarin gidan sarautar agadez manya manya,abinda zai gaya maka ya narkar da kansa,ya kuma maida kansa mallakin gidan sarautar halak malak. Hannunsa ya zura daga cikin babbar rigar,wadda kafin ita akwai riga da wando har iri biyu a jikinsa. Rigar farko daga wajen cikinsa ya zura hannu ya zuge wani zip,ya cusa hannun nasa,ya kuma ciro wasu takardu a nannade,abinda ya sanya tumbinsa komawa,ya kuma rage tudun da yake dashi. Zubewa yayi a qasa yana miqa mata takardun da dukka hannayensa guda biyu,ta saka hannunta guda daya ta karba zuciyarta na wani motsi da fatan ganin abinda takeso ta gani din,sannan ta soma warwaresu cikin dauki tana dubasu daya bayan daya. Wani irin murmushi ne ya subuce mata,wanda kana kallon fuskarta zakasan yayi nisa da zurfin da ya taba zuciyarta sosai. Tsaf ta kammala dubasu,sannan ta daga kanta tana duban tamim. "Na jima banga mutum me hatsarinka.......na jima kuma ina tunanin kalar sadaukarwar da zanyi maka.......saidai nan gaba kadan.......lokaci taqaitacce kawai nake jira na baka zabin abinda kake so na sadaukar maka dashi.....domin kuwa ka cancanci komai tamim" Wani irin murmushi yake yana gyada kai. "Ina nan ina jiran wannan ranar.........ina kuma me baki tabbacin daga randa na zabi abun sadaukarwa......kuma kika sadaukarmin din......na rantse miki harga Allah daga ranar zan damqa rayuwata da numfashina dukka a hannunki" Ya fadi yana dunqule hannunsa gami da dukan qirjinsa. Wani amintaccen murmushi ta saki. Alwashinsa kadai ya sake rura mata wutar son akai gabar da zata tambayeshi ta kuma bashi dukkan abinda takeso. Tamim nata ne zata iya cewa,tsahon shekaru masu yawa yana bauta a qarqashinta,bai kuma taba bijirewa umarninta ba. Batasan iyakar adadin umarninta da tamim ya cika ba,daga randa ya zame mata bawa zuwa yau,bata da wannan lissafin. Batakai ga cewa komai ba muryar yalwa ta ratso gurin. "Anyimin izinin shigowa?". "Anyi miki" Mammina ta fadi tana nannade takardun da kyau gami da maida dubanta ga bakin qofar. A ladabce yalwa ta qaraso,ta kuma zube gaban mammina wadda ta kafeta da ido. "Komai ya lalace Allah shi dafa miki,komai bai tafi yadda ya kamata ba" Dubanta sosai mammina keyi,saidai izzarta ta hanata tambayar yalwa komai,tana ganin ita din ba sa'arta bace. "Allah ya baki yawan rai.......shima tayi watsi dashi yadda ta saba......wannan karon ya samu tsaraba mafi girma da ba wanda ya taba samun irinta......tsarabar mari". Waje mammina ta fidda idanunta,cikin matsanancin mamaki. Yayin da tamim ya runtse idanunsa dukka biyun da kyau yana hasashen wani abu. "Garin yaya haka ta faru yalwa?,kina ina?" Mammina ta sake tambayar yalwa din. Qasa yalwa tayi da kanta,a sanyaye ta furta. "Gefan mayafinta ya riqe ranki ya dade". Da sauri ita da tamim suka zube mata idanuwansu,shuru ya baqunci gurin,kafin mammina ta gyada kanta. "Yayi kuskure ba qarami ba,amma kuma hakan ma yayi......ki kiramin laraba,taje ta duban halin da take ciki a sassanta,ina buqatar fara zuwa ganinta,ina buqatar fara ganinta kafin kowa,don nasa nan da awanni kadan tabbas sultane zai buqacu ganinta". Kai yalwa ta girgiza sannan ta miqe ta juya tana fita. "Tamim" Ta kira sunansa,abinda ya sanyashi daga kansa daga sunkuyon da yayi. "Ina buqatar wanzuwarsa a wannan duniyar tamu kaman kowanne dan adam,ina buqatar rayuwarsa tahau saiti.......kwanaki satittika ko kuma watanni kadan masu zuwa zamu samu buqatuwa da wannan wanzuwar......da wannan sabuwar rayuwar". Kai ya jinjina sannan ya miqe cikin ban girma,ba tare da ya sake cewa komai ba ya juya yana ficewa. Guri daya ta zubawa idanu tana wani gajeran nazari,daga bisani kuma sai ta fara gyada kanta a hankali qaramin kwantaccen murmushi yana subucewa daga fuskarta. *SHEIKH HAISAM* Tun a cikin motar da hambal ya dawo da kansa ya daukeshi bayan tattakin da yayi daga cikin masarautar agadez din har zuwa inda yace su jirashi baice da kowa komai ba. Tsakanin maher da hambal din suke hira kadan kadan kan yanayin garin da kuma al'adunsu. Fiye da rabin hankalin hambal din yana kan haisam,kamar yadda maher shima hankalinsa ya karkata ga haisam din. Wannan mode din ba dashi ya shiga agadez palace ba,to amma sunsan halinsa. Idan ba yaso bane fadi maka abu,bai fiya son a tambayeshi ba,wannan ya sanya suka ja bakinsu sukayi shuru. (08187255862 lu'u lu'u paying) Mintuna kadan suka iso gidan,wanda da sauri daya daga cikin hadiman gidan ya matso ya bude masa qofar. Qafafunsa ya zuro waje yana cewa. "Kuyi alwala,zan fito yanzu mu wuce masallaci" Ya sauke qafafunsa yana takawa a nutse zuwa cikin gidan. Har ya isa bedroom dinsa bai hadu da kowa ba,tunda dama sassan mallakinsa ne,sai omari da suke zaune tare kowa da shiyyar dakunansa. Baiga omari ba,kuma baya cikin mode din tsaiwa tambayar inda yake,sai ya rage cloak robe din jikinsa ya ajiye,ya zare rawanin kansa a hankali ya ajiye saman dressing table,abinda ya bawa sumarsa me santsi damar bayyana wadda ke kwance saman kansa cikin wani irin tsari. Fadawa idanunsa sukayi kan fuskarsa,fuskar da tayi wani fresh tayi tarwai saboda tsananin hutu da kuma kulawa,kawai sai ya samu kunnuwansa da dawo masa da sautin marin kamar a sannan aka yishi. Almond eyes dinsa ya bude sosai cikin madubin,yana son ya gano wannan sautin dama shine abinda yayi masa tsaye a rai tun dazu?,ashe shine abinda ya dunqule masa a wuya yaqi kuma wucewa?. Ta yaya d'iya mace zata daga hannu ta mari namiji?,namiji ma baligi Aaqili?. Imagine ace noory ko rumaisa ne zasu aikatawa wani haka?,waninma da yazo ganinsu da shirin auren sunnah. Wani mahaukacin tsaki yaja kamar zai tsinke harshensa. Ta yaya ma hakan zata faru a masarautar oromo?. Ta yaya suma zasu fara aikata hakan?. Ya tabbatar daga shi har nanay sun musu wani irin horo da babu yarinyar da zata iya soma kwatanta hakan,sai yaja da baya yana jin yadda ranshi ke motsawa,irin abinda a dazun baijishi ba sai yanzu,ya fara tattare hannun jubah dinsa yana tafiya a nutse zuwa toilet. Alwalar daya daura ne kawai ta bashi relief,dama kuma yana cikin dabi'unsa,duk yadda yakejin fushi cikin ransa muddin zaiyi alwala to zai samu sassauci cikin ransa( a duk sanda kike jin fushi kije kiyi alwala,in sha Allah zakiji sanyin ruwan yana ratsa har zuciyarki). Suna takawa zuwa masallacin dake layin,wanda qananun taku ne kawai zai sadaka dashi zuciyarsa na sake yi masa tariyar yadda al'amarin ya wakana. A lokacin ya gayawa kansa ne ba wannan ne ya kawoshi cikin masarautar ba.......ko meye zasuyi daidai da tsarinsu ne da rayuwarsu,aiki ya shigo yi,shi ya dameshi,kuma shi ya kamata ace ya kula dashi,amma baida jib'i da komai na rayuwarsu,sai gashi a yanzun yana jin kamar ba haka ba,abun yana neman tsaye masa a rai. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 49 ___________________________ *_INA MASU BUQATAR QAWATA GIDAJENSU DA KALAR TSUNTSAYE DON ADO DA DEBE KEWA?_* *_INA MASU BUQATAR FARA SANA'AR SAIDA TSINTSAYE.....SANA'A ME TARIN RIBA DA ALBARKA DA KUMA SIRRI A CIKINTA?_* *HALY JASHERU VENTURES.* munada tsuntsaye na kasashen waje masu kyau da daukar hankali kmn haka. TATTABARU French modain(Argentina) Indian faintail (3in1) indigo,opal,Andalu,Lahore,busa,Bukhara, indomie,Jacobin dasauransu. KAJI. Brahma,silkie,silver lace,coshine,dawisu, parrot (aku)dasauransu. , Munada kayan Islamic center.habbatus saudah,hulba,zaitun,qusdul Hindi,minannas,Rose water dasauransu,dangin garinsu ,mansu yayansu ,ganyensu. munada original Zuma,yar chad da mombila. Munada kayan gwanjo masu kyau daga jariri zuwa babba, Overall,Rumpers, bodysuit, sweaters,wanduna, tracksuit dasauransu,munada kaya masu kyau na bacchi na gwanjo. Munada Ethiopian magic hair oil 🪔 Wanda yake Kara gashi,yayi tsaho laushi,yayi Baki drct daga Ethiopian muke kaisa ko Ina afadiin duniya. Don Neman Karin bayani number waya 07046665338. ____________________________ *AKHNAN* Ko kafin takai ga idar da sallar taji an mata knocking ya kusa sau biyar. Tana sallan amman ranta yana baci. Ba wanda take buqata yanxu haka a kusa da ita,ba wanda take buqatar tayi magana dashi,kebewa kawai take so,sai kuma jiran kiran sultane. Kiran da inda tana da dama tabbas da zata tsere masa ne,amma kuma tasan bata da damar hakan,hakan kuma bame yiwuwa bane. Dole ne ta amsa tambayoyin sultane,dole ta tsaya ta fuskanci sultane muddin tana neman 'yancinta,dole ta masa bayani ta yakice kowanne irin tsoro dake a ranta. A hankali ya fado mata a rai sanda take zauke daidai saman daddumar,tafukan hannayenta akan saman fuskarta. Wancan lokacin da kalmar. "Subhanallah" Ta fita a bakinsa,sanda take dab da shan qasa daga saman thunder dinta. Har yanxu wannan sautin yaqi barin kunnenta,har yanzu wannan sautin ya sha tashinta daga baccinta a darare masu yawa. Tasha sake ganin wannan abun daya faru yana sake maimaituwa a cikin baccinta. Qamshinsa da har yanzu bata sake jin makamancinsa ba,har kwanan gobe tana iya hakaitoshi,saidai kuma da tarin wata irin matsananciyar tsana da kuma jin haushi. Inda tana da hali,tana kuma da dama lallai da sai ta laluboshi a dukka inda yake a fadin duniya. Tana da wannan qudurin,amma kiran sultane da maganar da sukayi a jiya kawai ta warware duk wani karsashi da take dashi. A yau kawai tsanarsa ta ninka a zuciyarta ninkin baninkin. Shine silar duka wani hukunci da sultane ya dauka a kanta. Shine sila,ta tabbatar wannan video clip din ya gani........ya kuma zame mata dalilin wannan horon da sultane yake shirin yi mata. Ta sake yadda abun shiryayye ne,dama ya shirya ne kawai don yaci mutuncinta ya kuma ci zarafinta. Tunda ga shaida da alamu dukka ta gani,ta tura musu request tana son a sake shirya wasan,amma sun maido mata amsar wannan dan wasan isn't available.......amma idan tana da sha'awar sake yin wasa,akwai tarin 'yan wasa available da zata iya karawa dasu. Bata da buqatar ko daya a cikinsu,tana buqatar karawa da shine don cire masa dukkan wani abu da yakeji a kanta......don cire masa tunaninsa na yayi nasara akan akhnan muhammad hammud..........da wannan tunanin ta wayi gari,saidai a yanzu sultane na shirin dakushe wannan shirin,ya kuma maida akalar tunaninta kan wani abu na daban. A karo na uku da aka buga qofar saita miqe a fusace ta isa qofan da kanta maimakon tayi amfani da remote ta bude. Cikin ranta tana me cin alwashin ko waye saita wanke masa fuska da zafafan mari tukunna,ko waye.....koda falaak ce,saidai kuma tana bude qofar sai taci karo da fuskar da tafi qarfin mari a gurinta. Mammina ce a tsaye yana fuskantar qofar dakin. Dukka wani yanayi na alhini rashin jin dadi da kuma damuwa gashinan kwance saman fuskarta. Jiki a sanyaye ta saki qofar tana komawa ciki,mammina ta biyo bayanta. "Don meye zaki kulle kanki akhnan?,bakya tsoron lafiyarki?,ko bakya tsoron wani abun ya sameki?" Ta fada tana riqo dukka hannayenta cikin tsantsar kulawa. Blue eyes dinta da suka rusuna ta waiwayo yana zubewa mammina su,tana ji a ranta har tsakiyar zuciyarta.......bata da wani sauran gata daya rage mata a duniya bisa dukkan alamu idan ba mammina din ba......sultane ne taqamarta na farko,to amma kuma alamu sun nuna kamar sultane din ya fara yi mata nisa,ya fara nisa da muradinta. Ba zatace ga a abinda yake faruwa ba kai tsaye,amma tana da yaqinin zai wahala idan ba MORSA bace ke shirin rusa wannan kyakkyawar alaqar ba. Duk wasu halaye da sultane ke gwada mata a yanzun baqi ne a tare da ita,tunda ta mallaki hankalin kanta bata taba ganinsa da wadannan dabi'un ba. Ci gaba tayi da kallon mammina kawai,abinda ya bawa mammina damar karantar abinda yake kai kawo a zuciyarta. "Tsoron me kike biftu?,kin manta alqawari na?......kina zaton idan sultane zai iya manta alqawarin dake tsakaninku ni zaituna zan iya mantawa?......duk runtsi duk tsanani ina tare dake akhnan" Sosai maganganun mammina suka karya mata zuciya. Bataso tayi kuka,don batajin ya kamata zuwa yanzu ta fara samun rauni har haka a zuciyarta,amma kuma tana buqatar kafadar da zata jingina da ita don samun sassaucin abinda takeji,don haka ta qara taku biyu,ta aza kanta saman kafadar mammina din. Hannunta ta dora saman sassalkar sumar akhnan dake da tsaho santsi da kuma sheqin baqi tana shafawa a hankali,kaman yadda uwa keyi ga qaramin yaronta da sigar lallashi. "Indai ina raye ba wanda zan bari ya aurar dake ga mijin da baki aminta dashi ba......ko baki fada ba yalwa ta gayamin.......sultane mahaifinki ne......indai ba zugashi akayi ba,bazai taba aurar dake ga mijin da baiyi miki ba......" Saita daga kan akhnan daga kafadarta tana riqe hannayenta dukka biyun. "Ki sa a ranki da mahaifinki kike magana.......ki bude bakinki ki gaya masa bai miki ba!". Ta qarasa maganar da wani sauti dake nuna akwai wani abu daban daya taba zuciyarta. Shuru akhnan tayi tana duban tsakiyar qwayar idanunta,irin duban da a yawan lokuta da dama yake qarfafa mata gwiwa tun daga yarintarta. Kallon idanun mammina din na bata wani irin qwarin zuciya tare da bata qarfin gwiwar aikata abinda take ganin bame yuwuwa bane ko ba zata iya ba. "Shirya muje.....ya aiko a kiraki,ni zan tsaya miki koda hakan yana nufin yin baqin jini,baqin jini a idanun sultane.......baqin jini a idanun morsa safiyyah". Zame hannunta tayi daga na mammina,iya Kiran sunan morsa safiyyah kadai ya sake harzuqa zuciyarta,sai ta juya da baya da sauri,ta kai hannunta kawai kan dogayen rigunan dake zube saman gadonta,wadanda dukkaninsu sabbi ne,birra ta soma gyarasu zata zuba mata a closet dinta tace ta barsu ta fice ta bata guri. Duk yadda take jin zuciyarta ta tsayu amma sai fargaba ta fara ratsata sanda suke nufar sassan sultane din. Tsinkewa kawai takeji zuciyarta tanayi zuwa pieces a cikin qirjinta. Ta fahimci hakan mammina.......saita damqe hannunta da suke cikin nata tana magana qasa qasa. "Karkiji tsoro......ina tare dake" Maganar data sake saukar da wani dan guntun sassauci kenan cikin ranta. To amma daga sanda mammina tayi sallama cikin parlor din sultane din,ta kuma hangi morsa safiyyah zaune a gefansa tana sake tsiyaya masa ruwan markadaddiyar apple sai taji tana neman rasa duk wani qwarin gwiwar tata saboda abubuwa biyu. Abu na farko yanayin fuskar sultane din. Wani baqon yanayi ne da sai me zuzzurfan kusanci dashi......me zuzzurfan hangen nesa da tsinkaye kuma shine zai iya karantar kwantaccen bacin ran dake kai kawo saman fuskar tasa. Duk da cewa ga me gajeran nazari wanda ba wata zuzzurfar alaqa Taakaninsa da sultane din zai dauka yanayi ne kawai irin na yau da gobe. Morsa safiyyah. ....wanzuwarta a gurin gabanin zuwansu ya sake rusa mata duk wani kyakkyawan zaton da ta shigo dashi. Ko sau daya......koda lokaci qwaya daya bata taba saqa alkhairi akan matar ba. Da yawan dagulewar al'amuranta tana alaqantashi da morsa safiyya din,alkhairi bai taba gifta mata ba muddin tana a gurin. Idanunta ta dauke a hankali tana lumshesu,tana kuma takawa zuwa ga sultane din bisa qwarin gwiwar mammina da kalaman da take gaya mata qasa qasa. Kalaman da ba lallai kai dake kallonsu kai tsaye ka dauka wani magana takeyi da ita. Cikin qasa da second uku wata irin shimfidaddiyar fara'a ta wanzu a fuskar mammina,idanunta tsakanin sultane da morsa safiyya. "Sannu da hidima" Tace da morsa safiyya dake qoqarin rufe tambulan din lemon data gama zubawa sultane. "Kece da sannu zaituna....." Ta amsa mata da salon daya sanya mammina jin wani iri. Kasancewarta mace me wata irin halitta da tasha banban data mata da yawa,irin matan nan da sukan iya shanye komai su kuma jure jin komai daga bakin wanda sukaso,saita maida mata da martanin murmushin,ta kuma qarasa a nutse daura da sultane tana yiwa akhnan mazauni daura dashi din,daidai sanda take cewa. "Muna neman sassauci da afuwa ranka ya dade........na shigo ba tare da ka nema haka daga gurina ba......zuciyar d'iyata cike take da fargaba da kuma zullumi,bata da qwarin gwiwar tunkarar mahaifinta sam a wannan ranar" Takai qarshen zancan tana zame yatsunta daga cikin na akhnan,ta kuma ja baya kadan alamun dake nuna tafiya zatayi. "Ina zuwa?" Sultane din ya tambaya kanshi tsaye yana ajiye tambulan din hannunsa. Duk da yadda morsa taqi jinin yadda dukkan wata kebantacciyar alaqa ko dangantaka data shafesu mammina ke ciki tsulum tsulum,amma ita kanta a yau din tafi buqatar zaman mammina akan fitarta. "Komai na d'iyarkin yanzu dake za'aci gaga da yinsa......domin shaida ta zama a wuyanki" Ya qarasa maganar yana gyara zamansa,irin zaman cikakken basarake,yana mata kuma nuni da kujerar dake kusa da morsa safiyya. A hankali ta dawo a nutse,taqi bari wannan murmushin nata yabar kan fuskarta,ta zauna a nutse tana fadin. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Lamarin d'a da uba koda mu iyaye ba kasafai aka fiya son saka kai a ciki ba......shi yasa ban tsaurara ba wajen son sanin laifin da ayau tayi ba". Ta qarasa maganar tana sadda kanta qasa a girmame. "Bana tunanin tsakanin wannan awannin abinda tayin zai buya daga idanu da kunnen sauran masarautu........" Yayi maganar cikin bagararwa,yana karbar toothpick daga hannun morsa wadda ta miqa masa,dukka tana yunqurin shanye abinda ke taso masa.......tana ta qoqarin shanye bacin ranta ne kawai da controlling din kanta. Wacce irin gurbatacciyar soyayya ce wannan?,wacce irin mayaudariyar qauna ce ta banza da wofi?.......wanne irin lullubin biri ne wannan?,wanne irin nau'in kisan mummuqe ne wannan?. Dukka lokaci daya morsa safiyya ta yiwa kanta wadannan tambayoyin daidai sanda take zube kallonta kai tsaye akan mammina din tamkar a fili tayi mata dukka wadannan tambayoyin. Tambayoyine da zataso ace ba cikin ranta ta furtasu ba,tambayoyine da take buqatar bayyanasu da sautinsa don sultane yaji........to amma kuma fitar tasu tayi imanin ba wani sauyi ko gagarumar rawar da zai taka da zata kawo irin canjin da takeso. A jikinta mammina din taji?,ko kuma tana shirye da karban kallo makamancin wannan daga gurin morsa din?,sai kawai ta daga nata idanun,suka kuma fada cikin na morsa safiyya. A cikin su biyun,ba wanda bai tantancewa kansa kalar kallon da dan uwansa yakeyi masa ba.......ba wanda bai qissima abubuwa da dama ba,amma kuma sai mammina din ta maye gurbin kallon da jifan morsa Safiyya da wani irin murmushi da ba komai cikinsa sai zallar nuna sanyi da rashin daukan abubuwa da zafi,sannna ta cire idanuwanta daga cikin nata,tana maida dubanta ga sultane din da ayau yake zaune cikinsu da fuskar da yake zama a fadarsa cikin talakawansa. "Ya kukayi da abood ramadan?" Ya jefa tambayar ga akhnan,wadda banbamcinta da tambayar awanni nawa ya rage ta mutu kadanne. Dame zata amsawa sultane?,bayan tayi imanin yasan komai.....ya kuma ji komai.......yanayinsa kadai ya gaya mata hakan. Shuru parlor din ya dauka,tamkar babu wani sauran ne rai daya rage a gurin. "Ya kukayi da abood nace!" Sultane ya sake tambayarta da wata irin tsawa data kada 'ya'yan hanjin dukka su uku dake gurin,saboda wata dabi'a ce dake baquwa ga dukka halayyar sultane din. "Bap......bapp.......iii" "Baiyi miki ba" Ya fadi bawai da sigar tambayarta ba......a'ah da sigar bada amsa ta kai tsaye. Sake yin qasa tayi da kanta tana jin kamar zata narke,tana jin dama qasa zata tsage mata tabbas da zata shiga ciki ta buya daga tuhume tuhumen sultane din. "Wannan shine ya baki qwarin gwiwar daga hannu ki mari baligin namiji?!!!!" Ya daka mata wata sabuwar tsawar,abinda ya sanyata curewa guri daya tana kuma cukuikuye mammina duk da dan nisan tazarar dake tsakaninsu. A lissafin rayuwarta gaba daya,sau daya tak zata iya tuna an taba mata tsawa. Tsawa......fada ballantana uwa uba dukka dukkansu wani abune sabo kuma baqo cikin dictionary din rayuwarta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 50 ___________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah ____________________________ "Bappi........" Ta kira sunansa da wani sauti da ya daki zuciyarsa a take kuma ya karyata,saidai duk da hakan bai bata koda space qwaya daya da zata fahimci hakan ba. "Karki sake kiran sunana........" "Afuwa ranka ya dade.......afuwa,a huce haka" Mammina ta furta cikin kwantar da murya,tana kuma tarairayo akhnan sosai cikin jikinta tana qoqarin daga Fuskarta. Hawayen dake malala saman Fuskarta ya sake karyasu,saidai tsakanin sultane da morsa safiyya ba wanda ya bata daman karantar hakan,yayin da morsa safiyya ke bin mammina da kallo,wadda ke qoqarin tsaida hawayen akhnan,nata idanun suna cika da hawayen da suka soma neman fitowa. Sosai mammina din ta rungume akhnan din,hawaye suna kubce mata. "Saketa ta gama amsa tamanyoyina!" Sultane ya fada cikin dakewar zuciya da kakkauran sauti,sai mammina din ta zame akhnan din daga jikinta,saidai kuma ta gaza sakin hannuwanta kamar wadda aka ce za'a rabasu. Idanu morsa safiyya ta janye,tana jan lahula wala quwwata illa billa a ranta. Komai tana ganinsa ne kamar almara,dabi'u da acting din mammina yana sake kashe mata duk wani karsashi nata. Daga sanda baqon yazo ya tafi,bata bawa armelle ko kowa na kusa da ita kowacce dama ba bare taji abinda ya faru. Fargaba ce taf ranta data hanata sakewa,sai kawai tayi amfani da wannan damar,ta shiga kitchen da kanta,ta soma hadawa sultane abinci kaman yadda takanyi lokaci bayan lokaci. Gurinsa takeson zuwa,amma bataso ta tunkareshi haka kai tsaye,don batasan ya zata taras dashi ba,wanne yanayi zata samu da zai bata hasken dukkan abinda ke faruwa?. Yadda ta samu fuskarsa duk da yadda yake qoqarin tarbarta da girmamawa amma gwiwarta ta sanyaya.......yanzun ta fahimci komai daya faru.....mammina kuma na sake kasheta da wannan salon nata......salon nan dai na shekara da shekaru.......wannan salon da take tunanin ya sanyata ta cimma gaci,gacin da a wajen morsa faduwa ce wanwar.......lokaci! Shine keda kowanne hisabi......shine gwanin bayyana komai. Dukkaninsu sun dauka sultane ya gama duk wata magana da zaiyin,amma kuma yadda bai basu izini ko umarnin tafiya ba ya tabbatar musu akwai sauran magana a ranshi. "Kin bijirewa abood?". "Tabata yaso yayi ranka ya dade.......taba akhnan babban zunubi ne kaima ka sani" Mammina ta furta tana sake yin qasa da kanta,saidai yanayin maganarta kadai ya nuna akwai zafi cikin maganar data fada din. Wannan karon kasa daurewa morsa tayi,ta daga kanta tana duban akhnan dake qudundune tana sharar hawaye,abinda ta mance rabon data gani a idanun akhnan. Kalmar ta yiwa kunnuwan morsa nauyi da girma,ta sake duban idanun mammina dake kallon qasa. Idan ita din uwace ga akhnan,kuma ya tabbata abood ya taba jikinta......shin zata bari duniya taji?,zata kuma gayawa wani maganar koda mahaifin da yayi silar zuwanta duniya ne?. Ga yarinya irin akhnan,fitar wannan lafazin mummunan batanci ne da kuma tabo da zai iya yaduwa yanzu yanzu kamar wutar daji. Ko daya maganarta bata zaunawa morsa safiyya ba.....duk duniya,koda mammina dake tutiyar ta raineta ta kuma girmar da ita bata tunaninta ta fita karantarta. Akwai wasu dabi'u na SAFEENA akwai wasu dabi'u na DIORY FAMILY da suke cikin jininta,wadanda suka cakuda da dabi'u da halayen SARAUTA cikin jininta. Bata tunanin akwai wani d'a namiji da akhnan zatayi doguwar tsaiwa dashi,doguwar tsaiwar kuma da zata bashi daman taba wani sashe na jikinta. Wannan halin nata shi kadai ne yake bata nutsuwa da kwanciyar hankali a zamanta a Niamey,banda wannan tabbas koda dawowarta agadez ta zauna kusa dasu yana nufin mutuwar aurenta da sultane......koda hakan zai zama silar daukar wuqa ga akhnan ta yanka wuyanta,to tabbas zatayi silar dawowarta agadez. Ta sani,tana da wani irin jin kai,tana da wata irin ajiyayyar izza da bata tunanin akwai wani namiji ma daya taba ganin koda singalalin hannunta bare jikinta,ballantana hakan ya zama sanadin da zaikai hannunsa jikinta. Akwai dai wani abu daban daya faru......amma banda zancan taba jiki. "Kin tsallake abood.....ina me miki albishir din kin rasashi kenan.......zabinmu na gobe zaizo gurinki.......daga sanda yazo kuma ki kalleshi da idanun da mace ke kallon mijinta.........wannan shine maganata ta qarshe dake". Sultane ya fadi. Wani irin nauyi taji kanta yayi mata,qamqam ta riqe mammina tana jin wani bala'i yana kewaya kanta. "Sultane bazai haqura ba?,ba zai haqura ba mammina......na rantse har yanzu babu irin mijin da........." Ya isa akhnan,ki godiya ki wuce muje" Ta fadi tana qoqarin dagata,yayin da sultane din yayi kaman baisan da wanzuwarsu a gurin ba,ya gyara kashingidarsa yana maida idanunsa ga tv din dake haska labarai daga France 24. Da wani irin kallo morsa ta daga idanunta tana duban mammina sanda suka fara takawa. "Zaituna" Ta kirata da yanayin da ya fusgi hankalin mammina din qwarai. Ta jima bataji wannan sunan saman harshen morsa safiyya ba,tun a wasu shekaru masu dan yawa can baya da suka shude. "Maganar taba jiki akan kowacce diya mace zubewar kima da martabarta ne.........inason wannan maganar ya shafe daka bakinki shafewa na har abada" Tayi maganar da harshe dake nuna gargadi. Wani irin zazzafan kallo ta zubewa morsa din tana kafeta da idanu. Sai kuma ta saki murmushi gami da sanyaya kallonta akan morsa din. "Kinfi gaban haka ai,kina iya bada umarni nabi,akhnan nan kuma diyarki halak malak,diyar da kinfini iko da kusaci da ita,ayimin afuwa" Ta fadi tana dan rusunawa kafin ta kama akhnan da zummar su wuce. Zamewa kadan akhnan tayi daga riqon mammina. "Me kikeyi na ba daidai bane?,ko yaushe baki iya ba?,ko yaushe kome zaki mata ba daidai bane?" Akhnan ta fadi a zafafe. Fes ya fahimci wannan fushin,wannan taurin kanne ya motsa,saita riqeta sosai "Indai na isa dake muje kawai" Ta fada tana duban tsakiyar idanunta. Wani sauka taji ta soma yi,ba musu ta juya a hankali tana takawa mammina na take mata baya. (08187255862 lu'u lu'u paying) Qasa da kanta morsa safiyya tayi,don taji dukkan abinda akhnan din ke fadi. Wani irin d'aci ke zarcewa maqogoronta tun daga saman harshenta,kalar d'acin da jinsa ya zame mata jiki,amma har yanxu ta kasa daina jinsa. "Safiyya" Sultane ya kirata a tausashe yana tsareta da ido. "Allah ya taimakeka" Ta furta a nutse tana motsa labbanta da tun dazun taji sunyi mata nauyi. Sarqafewa idanuwansu sukayi guri daya ita dashi,kafin ya janye nata idanun zuwa wani sashe na daban. Ya sani,shurun safiyya yana nufin abubuwa da dama,duk da cewa ba komai take iya yiwa shurun ba,ba kuma komai take iya ajiyarsa a ranta ba......amma muddin akace tayi shuru,to tayi shurunne,ba kuma zata qara magantuwa akan komai ba. Ta sani baiji duk abinda akhnan ke fadi ba,don sautinta bame qarfi bane duk iyakar inda takai ga yin magana cikin bacin rai,a daidai lokacin kuma hankalinsa ya tafi sosai akan wayarsa da batasan me ya janye masa hankali akan wayar haka karon farko ba. "In sha Allah......zan tabbatar da zamana mahaifi kaman kowanne uba.......in sha Allah" Ya fada yanason karanto wani abu ko yaya dake ranta. Sake daga kanta tayi tana sakin murmushi a hankali kafin tace. "Allah ya baka iko.....ya qarfafeka a dukka lamuranka" Idonsa ya lunshe shima yana gyada kai. "Ameen..........yaghana ta dawo.......yanzun nan suna filin jirgi". Wani murmushi ne ya subuce mata,wanda sam bata ma shirya fitarsa ba. "Alhamdulillah" Ta fada a fili walwalarta tana qaruwa. Watanni bakwai da sati shida kenan da barin yaghana masarautar agadez,watanni bakwai din da suka dinga zuwarma morsa safiyya da wani irin tsanani,bata taba zaton yaghana tana da wani muhimmanci me girma haka a rayuwarta ba sai sanda tayi nesa dasu. Duk da kusan cikin kowanne motsi da kai kawo a masarautar tana tare dasu,amma wannan nisan dai bai canza daga yadda yake ba. Yaji dadin yadda karon farko albishir dinsa ya saukar mata da fara'a d walwala,ya gusar da wannan yanayin daga fuskarta,sai yadan tsokaneta kadan. "Yanzu zami fara cike takardu kafin samun damar ganinki kenan,tunda yaghana ta dawo?" Murmushi tayi tana girgiza kai. "Duk muhimmanci da yaghana ke dashi,bana tunanin ta kama qafar naka". Shuru ya danyi yana jinjina kai,duk da yana kokwanto a maganarta. " Yanzu sai ina kenan?" Ya tambayi safiyya dake gyara babbar rigar da take ta'ammali da ita a duk sanda zata baro sassanta don sake suturce jikinta. "Ba wanda ya gayawa isowarta yau,ina tunanin harkai......dole akwai buqatar shirin gaggawa" Ta kammala fada tana rufe jikinta ruf zagayayyar fuskarta dake yawan tuna masa da safeena ta bayyana. Sai yaja numfashar cikin hunhunsa sannan yace. " A sauka lafiya" "Godiya nake" Ta furta cikin rusunawa ta juya tana takawa da wannan nutsuwar tata da ba abinda ya banbantata data safeena. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 51 ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ *AKHNAN* "Tayi nasara.......tayi nasara mammina......tayi nasarar shiga tsakanina da mahaifina,ki gayamin mammina.......wai da gaske ne?,da gaske ne wannan alaqar da kike cewa akwai a tsakaninmu?,da gaske ita din uwace a gurina?". Akhnan da Fuskarta ta sauya launi zuwa pink da sirki sirkin red ta fada tana takowa cikin izza ta tsaya a gaban mammina kai tsaye tana dubanta. Hannunta mammina din ta kama,a tausashe ta jata ta ajjiyeta saman sofa bed,sannan ta jawo ottoman ta zauna akai tana dubanta. "Babu wani kuskure ko qarya a cikin abinda kika sani,abinda kika sani din dai shine xan yita maimaita miki.......biftu,ba buqatar ki damu da kowa a duniya muddin mammina dinki na tare dake.......ba buqatar damuwa da kulawar kowa indai mammina na nan..........maganan sultane ta gobe kada ta razanaki.......kada tasa ki rasa wannan izzar taki.......kar tasa ki manta matsayinki,kada kuma tasa ki manta ke wacece..........idan bakisonshi shima,hakance zataci gaba da tabbata,ba wanda zai canza ko ya kaiki bigiren da bai dace da ra'ayinki da tsarinki ba......ki daina dimauta.......ki nutsu kici gaba da tuna matsayinki......ki nutsu kici gaba da riqe wace ke a ranki". Wani ajiyar zuciya ta sauke tana son ta koma saitinta kamar yadda mammina ke buqata,saita harde hannayenta a qirjinta,tana zuqar iska tana fesarwa a hankali tanason saisaita zafin da zuciyarta takeyi. "Da kyau......." Mammina ta fada tana sake riqe hannunta da kyau. "Babu wani da zai canza wannan soyayyar......ba wanda yake da qarfin jirkitata koda morsa safiyya ce" Ta sake fadi cikin son bawa akhnan din dukka qwarin gwiwa. *HAISAM* Ba dabi'arsa bace kaiwa nisan dare har haka kafin yaci abinci,amma a ranar sai a qalla kusan tara na dare ya zauna cin abincin dare. Addisaleem ne tsaye gaban table din,ya bude dukka warmer din dake dauke da nau'in abinci kala biyu,abun sha guda daya sai coffee,sai kuma hadin salad guda biyu,don qa'idarsa ne,ko meye zaici sai ya tabbatar akwai ganye da fruit a kusa dashi. Duka nau'in abincin dake kan table din kalar abincin yaren oromo ne da haisam din yafi so. Addisaleem ya qarasa shirya komai,yaja baya cikin girmamawa ya basu guri shida omari. Shuru gurin yayi,don ba kasafai yake magana ba idan yana tsaka da cin abincin. Ruwa omari ya dauka yasha ya ajiye,ya kasa haquri kuma ya kasa shuru jin baice dashi komai ba,sai yayi dan gyaran murya kadan. "Ya ranar farko ta kasance cikin masarautar agadez?" Yayi tambayar yana kai lomar abinci bakinsa. Zagayayyun almond eyes dinsa ya daga ya dubi omari,sai ya lumshesu hadi da janyesu,ya kuma nunawa Omari plate dinsa kawai ba tare da yace komai ba,yaci gaba da cin abincinsa a nutse. Murmushi Omari ya saki yana maida hankalinsa ga abincinsa. Alamu dukka sun nuna yau mutanen ne a kusa,'yan miskilanci,shi kuma labari yakeson ji. Yanason yaji ya nasu gidan sarautar yake?,meye banbamcinsa dana jimma?.....dame yafi nasu,bazai qyaleshi ba kuwa sai yaji. Bai samu wannan damar ba hussam yayi kiran haisam din a waya,sai ya ture abincin kadan,ya daga wayar ya karata a kunnensa "Hello" Hussam ya fadi yana tattara hankalinsa a jikinsa. Dif haisam yayi masa yana shafa sumarsa gami da dan lumshe idonsa,duk da ya bashi alama da zata saka ya fahimci yana jinsa. "am dhiifama(ina bada haquri),assalamu alaikum warahmatullah" Hussam ya gane kuskurensa da kansa ya kuma gyara. Ya manta sam haisam din baya daukar dabi'ar hello,kusan dukkaninsu sun saba da fara furta sallama a waya kafin komai,kuma duk ta dalilinsa ne hakan. "Wa'alaikumussalam warahmatullah" Ya amsa masa da muryarsa data sake wani irin sanyi,yana jin dukka gabbansa sun gaji,duk da ba wani abun azo a gani yau din yayi ba. "Kana lafiya obbo?" "Alhamdulillah.........ya nanay take?" Ya tambayi hussam din. Yaso kiran nanay yaji lafiyarta,yau duka basuyi waya ba,to amma bayason yayi magana da ita lallai zata ji muryarsa ba yadda ta saba ji ba,kuma yasan halinta sarai akan duk abinda ya shafi yaranta,yanxun nan zata shiga damuwa. "Tana lafiya obbo.......yanzun muka gama magana da Mr Hambaa......." "Tole(alright)........ina jinka". "An fidda ribar turaruka na kamfanin SHEBA SCENT da SELAM PERFUMES......." "Uhmmm" Haisam ya fada a nutse yana sauraren hussam. Qaramin dariya hussam ya saki. "The amount is incredible obboo......wannan shekaran ya kamata kayi aure " Ya furta yana dan danne murmushinsa. Bayaso haisam yaji,yana kuma son ya fahimci da gaske yake maganan. "Hussam......are we age mate?" Ya fadi da seniority dinnan nasa da wani lokaci yakanyi amfani dashi akan hussam din,don hussam din ya cika wasa. "Dhiifama" Ya fada yana gyara mode dinsa. Zamansa haisam din ya gyara yana duban wayar. "Ka zauna lallai a qarasa sauran lissafin daya company din,a fidda zakka da sauran kudaden da aka saba fitarwa,ragowan ka saka a account din nanay". Idanu hassam ya zaro dukka waje. " Account din nanay obbo?". Ido ya lumshe sannan ya bude. "Bakaji bane na maimaita?". Kansa hussam ya sosa. "Naji captain......amma kuma,the amount is too large obboo". "Nikam hussam......akwai wata shawara da nace ina nema daga gareka ne?" Kai ya girgiza da sauri,don tuni ya fahimci inda haisam ya dosa,bai sake cewa komai ba,har haisam din ya zare wayar ya kasheta yana fesar da iska. "Baka ce komai ba har yanzu?.....ko akwai wani abu da ba daidai ba?" Muryar Omari yaji daga bayansa yana tahowa. "Ya salam" Ya fadi a fili,abinda ya bawa Omari qaramar dariya kenan,ya dawo gabansa ya zauna. Idanunsa da suka shanye kaman wanda bacci ya fara kamawa ya zubawa Omari,kallon daya sanya Omari fahimtar yau dai akwai abinda ya taba masa rai. "Ba wani labari Omar,idan akwai zakaji" Ya fadi yana miqewa gami da kwasar wayoyinsa. "halkan gaarii(goodnight)" Omari ya fadi cikin sauqaqewa kansa yana miqe bayansa cikin sofa din gurin,ya fidda wayarsa don rage wani aikin. Bazai tsaya jayayya da haisam ko damuwar sai yaji komai ba,yasan halinsa shima ya iya hutsancewa wasu lokutan,musamman akan abinda bai shiryawa yi ba,shi yasa ya sauqaqewa kansa wahala na barinsa ya tafi. Duk wani haske na dakinsa ya rage yabar na gefan gadonsa. Littafi biyar yana daukowa yana sauyawa amma duka yau sai yaji bayajin karsashin karatun,sai kawai ya miqe yana zura lausasan slippers dinsa,ya dauki wayoyinsa ya sauka a hankali zuwa library. *MAMMINA* Duk da kasancewar yanayin na shigowar dare da kuma fara nisansa,don a qalla sha daya ne harda rabi na dare,amma hakan bazai hanaka ganin qawatacciyar rigar dake sanye a jikinta ba. Doguwar riga ce irin ta asalim larabawan saudiyya data kasance free size me fadi sosai,wadda keda wani irin adon duwatsu masu kyau da daukan hankali da kuma adon zare mabanbanta. Daga saman rigar wani yalwayaccen mayafi ta sanya da yake kama da hijab kalar data dace da rigar jikin nata. A yanayin duban da zaka mata na farko zaka fahimci shigar bata dace da irin shigar da takanyi cikin gida ba,bata kuma dace da shigar da takeyi a lokaci irin wannan ba. Yadda gidan ya dauki shuru sai sassanta ya zaman shurunsa yafi na ko ina,don ta jima da bada umarnin tafiyar dukka wani hadimi zuwa makwancinsa,idan ka dauke hadiman dake tsaron qofa bayan qofa da zaka yita wucewa har ka iso babbar qofar da zata sadaka da sassanta. Su biyu ne rak a dukka manyan falukan nata,ita da kuma amintacciyar hadimarta yalwa,wadda ke zaune kanta a qasa tsakanin kujerun falon. Tayi kai kawo tsakanin falukanta har batasan adadi ba,har bata duban yalwa dake zaune ba tare da wani qwaqqqwaran motsi ba,da alama tana cikin irin yanayin da uwar dakin nata take ciki ne. (08187255862 lu'u lu'u paying) A takowar da mamminan ta sakeyi ne yalwa taja numfashi gami da daga kanta. "Allah ya baki yawan rai,sai nake ganin kamar daren ya tsawaita.........kamar dadewar tayi yawa,tafiya daga cikin saharar camaroo zuwa nan baikai ace ta dauki lokaci me tsaho irin wannan ba......" Yalwa ta furta cikin alamun nuna damuwa sosai. Hannayenta ta goye a qirjinta,a hankali ta qara taku biyu sannan ta zauna hannun kujerar dake kusa da ita. "Akwai qarin jami'an tsaro da 'yan sanya ido a tsakanin dukkanin saharorin dake kewaye damu,saboda dalili na tsaro da ake fama dashi,saidai kuma bana tunanin zaya bari su biyo ta irin wadannan hanyoyin.......don shi din masanin dazuzzuka ne da barayin hanyoyin cikin sahaara" Ta fadi damuwa fal muryarta. Sake duban agogon dake gefanta yalwa tayi,sannan ta sake daga kanta tana kallon mammina. "Allah shi baki yawan rai,yanzu mene abun yi?" Ta qarasa maganar tana sake rusunawa,duk da cewa daga zaune take. Sakin hannayenta tayi,ta miqe tana furzar da iska daga bakinta gami da yin taku uku. "Ko meye zai faru yalwa.......a daren nan nakeso almaz ya kasance cikin qasar agadez......babu wata rana da tafi dacewa da dukka shirina irin wannan ranar......irin wannan lokacin......irin wannan daren kuma,don ina ganin wani haske da dacewa,wanda banaso wannan sa'in ya kubce daga cikinta..... Ki lissafamin bugawar mintuna sittin cif......awa guda kenan,idan ba wani motsi zan bibiyi komai,koda kuwa da kaina ne" Ta qarashe maganar tana miqewa tsaye,gami da hada hannayenta guri guda. Daidai da bugawar mintuna sittin din cif cif,wanda ya dace da qarfe sha biyu da mintuna ashirin da bakwai na dare wayar da bata ringing saidai qara ta cilla haske. Da sauri yalwa ta daga kai tana kallonta. "Tamim ne" "Daga" Ta bata umarni a taqaice tana tattara hankalinta. Sauraron abinda ya fadi kawai tayi ta gimtse kiran,fuskarta a washe da fara'a ta dubi mammina. "Anyi nasara uwar dakina" Idanu mammina ta lumshe tana sakin wata ajiyar zuciya me nauyi. "Suna ina?" "Unguwar daura......" "Ina buqatar haduwa dasu" Ta furta tana duban yalwa. Idanu yalwa ta fiddo waje tana dubanta. "Ranki ya dade.......kinsan dokar fitarku daga cikin masarauta ai,ballantana fitar ma irin wannan lokacin?,irin wannan lokacin ma a aiki irin wannan dake buqatar dukkanin sirri da takatsantsan?". Kai mammina ta girgiza. " Bazan fahimci kowanne bayani naki ba yalwa.......bakisan waye almaz a guri na ba......." "Allah ya baki yawan rai,da kinyi haquri zuwa safiya,sai muyi tunanin ta yadda zamu shigo dashi cikin gidan ba tare da kowa ya sani ba.......amma bana tunanin akwai wata hanya guda daya da zaki iya fita wadda babu masu tsaronta a ciki,ba tare kuma da koda su sun ankara ba" "Me yasa wani lokaci kwanyarki kamar tana rage kaifi?......me yasa wani lokaci kamar tana rage gudu me makon ta qara?" Tayi maganar tana soma zare mayafin kanta Idanunta akan yalwa. Qasa tayi da kanta,tana kasa cewa mammina komai,don ta kasa gane hikimarta kwata kwata. "Tashi ki kiramin ayaana.......kice ta taho da tufafinta guda daya da kowa yafi saninta dashi" Mammina ta fada tana komawa saman kujerar ta zauna hankalinta kwance zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 54 *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX A hankali ya saki handle din daya kama dazu,tunaninsa yana dawowa baya kadan. Hoton kayan ya sake gilma masa,take Muhammad hammud palace ya dawo masa. A hankali yake jinjina kai.......tabbas kayan na masarautar ne.......amma kuma ba wani abu da zai bashi daman zurfafa tunaninsa,duk da cewa cikin jikinsa yakejin kamar akwai wani abun na daban. ★★★★ Cikin takun dake nuna zallar qasaita da kuma nutsuwarta take takawa cikin filin da yake da fadi da wasu lafiyayyun grass carpet,wanda aka tsarashi aka kuma tanadeshi ne kawai saboda ita din,saboda jin dadinta,da kuma yadda ta kasance ma'abociyar son wasannin motsa jiki kala kala. Tayi kyau cikin wata irin kyakkyawar over sized sweet shirt fara qal me ratsin adon royal blue,wadda ke hade da wani skirt da duka duka tsahonsa qaurinta,don baikai idon sahu ba. Tsaf ta daure gashinta a tsakiyar kai da wani farin ponytail holder da aka qerashi da wasu irin fararen duwatsu masu daraja,jelar gashin ta tsaya a tsakiyar kanta tana lilo daga hagu zuwa dama saboda yanayin yadda take takawa kamar wani qasaitaccen dawisu. Leggings ne a jikinta wanda yabi jikin nata sosai ya kuma fidda qirar shape din da Allah ya bata da wadatattun cinyoyin da ba zakace nata bane,wadanda suka sake fidda shape dinta sosai. wani siririn scarfs ne kawai data dan lullube saman kanta dashi wanda ba komai ya rufe mata na gashinta ba. Hannunta tana dauke da wasu irin hockey sticks guda biyu farare masu kyau. Ma'abociyar son abubuwa ne farare,don kusan komai nata zai wahala ka cire farin kala a ciki. Birra,buhaina bushira da bara'atu ne a bayanta,birran na dauke da wani babban back pack da tarkacen kayan hockey dinta ke ciki,bara'atu kuwa water bottle ne a hannunta da wani silver vacuum flask me wani irin Royal colour,sai bushira da ita kuma ke riqe da dan qaramin kyakkyawar jakar towel dinta. Ta jima bata buga wasan ba,don su kansu sun manta lokaci na qarshe da tayi wasan. Itama tasan hakan,abubuwa sun mata yawa akai da yasa ta dade rabonta dashi,amma a yau din nishadi take nema........tana neman abinda zai dauke mata hankalinta ne daga dukkan wata damuwa da kuma tsimayin jiran isowar baqon da QADDARA tasa ya zabi ganawa da ita a yau. A irin wannan yanayin cikin tsaro take kasancewa shi yasa take duk kalar shigar da take so bisa yaqinin koda a mata sai wanda ta amince zai iso shiyyar da take ballantana maza. Ba wani namiji da ya isa ya rabo koda hanyar sassanta ma ballantana ya shigo mata. Cikin sanin aikinsu suka dire mata komai,ta zauna a hankali tana gyara madaurin snickers din qafarta,sannan ta zari hockey stick dinta guda daya gami da miqewa,birra dake dauke da ragowar balls din ta biyota a baya gami da tsaiwa agurin data saba tsaiwa din a duk lokaci irin wannan. A nutse da kuma wata irin qwarewa ta fara buga wasan. A hankali zuciyarta dama jikinta ya fara sakewa,ta fara samun nishadin da take muradin samun,saidai bata jima sosai ba muryar shehnaz ta sauka a kunnenta. A nutse ta waiwayo ta kalli shehnaz kadan kafin ta maida hankalinta ga wasanta. Dukkaninsu haushinsu takeji ita da aisa din,amma tayi targeting lokacin da zata maida musu magana. A nutse shehnaz ta rage jayan jikinta,sannan ta dauki sandan hockey dayan daya rage tayi joining akhnan. Jeki mutu akhnan din batace da ita ba,bata ma sake koda kallonta ba amma ta ware da buga wasan da daga qarshe ta bawa shehnaz kashi sosai. Yarda sandan tayi ta koma baya a hankali bayan wasan ya kammala,ta zauna tana karbar towel daga hannun barratu tana goge qura da dan gumin da jikinta ya fara yi. Hakan ko kadan bai damu shehnaz ba,tayi joining nata ne kawai don tayi making nata farinciki ko yaya ne. Ba jiya ko yau ba,dukkaninsu a dukka wani wasa da za'a buga,tun zamanin quruciya har yau ba wanda yake buge akhnan din,sun saba da wannan,idan kaga an cinyeta to d'ai d'aikun wasan da bata iyasu ba,a nan ma sakar musu take,bata fiya yarda a buga wasan da ita ba ballantana a cinyeta. Ta saba koda yaushe nasara tana bangarenta,ba kowanne lokaci bane take daukan rashin nasara tayi haquri dashi ba. "Nanniee tace tunda tazo bata ganki ba......tanata kuma aiken kizo,ko saqo bai sameki ba?" Shehnaz ta fadi idanunta akan akhnan tana zama kujerar dake facing dinta. Sai data sha kusan rabin ruwan kafin ta miqawa barratu,tasa hannu da sauri ta karba tana rufe bottle din. Blue eyes dinta ta zubewa shehnaz kafin ta janyesu tana rage musu girma. "Zuwa kukayi daukan gawata kenan?,an gaya muku sultane yayi layya da nama na ne?" Ta fadi da wani irin taushi saidai a tsakiyar muryarta da zancanta zaka fahimci da yanayi na jin haushi take maganar. A nutse shehnaz ta dauke dubanta daga kan akhnan din. Bata shirya gaya mata komai ba a yanzun,don zai zamana kamar qarin rikita mata lissafi ne kawai. Duk da akwai buqatar su zauna da ita,akwai buqatar sanin da saninta komai yake tafiya a sahel couture ko kuwa?. "Me kuma yanzu akayi miki?" Shehnaz ta fadi duk cikin neman hanyar da zata gusar da fadin ainihin dalilin rashin tahowarsu akan lokaci ita da aisa din. Kaman akhnan din ba zata daina kallonta ba,sai kuma ta zare idonta daga kanta tana jin bata da lokacin bawa shehnaz amsar komai. Duk da cewa tare suke takawa suna kuma komawa zuwa cikin gidan amma ba wanda yace da dan uwansa komai,daga qarshe suka rabu a mararraba,akhnan tana wucewa sashenta gami da bawa buhaina saqon ta aikawa nannie tace mata zata shigo. Kafin ta gama hutawa a rest room dinta tuni barratu ta hada mata lafiyayyen ruwan wanka kaman yadda suka saba. Ruwan wankan da kullum ake shiryashi hawa biyu. Na farko ruwan ganyan gwanda ne daya zame mata abokin rayuwa dana ganyen lalle,wanda akayi packaging dinsa ake mata order dinsa tun daga qasar china. Kowacce safiya ganyen gwanda shine abu na farko da ake dafa mata ta shashi a matsayin tea(anti aging ne,indai bakison tsufa ki gwada shansa kullum da safe,yana hana tsufa da gyara fata sosai). Mayukanta na amfani dukkaninsu organic ne daga mayuka na asali irinsu man kwakwa da sukanzo a mazubi me kyau da tsada,a kuma batar masa da kamannin da zaka kasa tantance wanne irin mai take amfani dashi?. Wani irin kyau na musamman fatarta take dashi,kaman yadda glowing din skin dinta yasha banban dana mutane da yawa,zaka tara mutane sosai baka samu me fata me sulbi da jan hankali irin nata ba,wannan yana daya daga cikin abubuwan da yasa take alfahari da kanta,take kuma sake kula da jikinta tare da bashi wani irin tattali da muhimmanci. Mintuna talatin ta dauka kafin ta fito,ta zarce zuwa spa room dinta,dakin da aka ware na musamman da dukkan wasu nau'ikan gyaran kayan jiki da 'ya mace zata buqata dan qarawa fuskarta da fatarta kyau dama jikinta gaba daya. Idan ka kalli dakin zaka dauka an wareshi ne don yiwa hamshaqan mata gyaran jiki,irin tsadajjen gyaran jikinnan me aji da kuma tsada da daraja saboda yanayin kayan aikin da aka ajjiye a gurin. Wani abu ne daya zame mata jiki duk qarshen kowanne wata,tana ware rana irin wannan ta shiga body steamer machine ta tsuma jikinta sosai da sassanyan turarukan da batasan daga ina aka samar dasu ba. (Asalin turarukan INCENSE BY KABO DAUGHTER,masu tsananin kama jiki da muhalli da wani irin tattausan qamshi,tasted and trusted,ba tallan molanka bane +234 803 211 9803). Wasu awanni biyun ta sake batawa wajen maintaining jikinta da gyara,bayan ta shafe kanta da kwababben lalle shima da wasu sinadarai na musamman. Dukka wadannan din sun zame mata jiki,ta tashi dasu tun batasan darajar abun ba a gurin mammina.......asali daga wajen morsa safiyya aka fara mata,saidai rashin sakewarta da morsa safiyyan ya sanya ta miqa komai ga hadimanta da kusan dukka rayuwarta da kulawarta ta lura a hannunsu take,su kuma suna rayuwa da ita ne cikin sassan mammina din. Sosai mammina ta riqi bada umarnin yi mata gyaran hannu bibbiyu,har ta girma yazo ya zame mata jiki. Wannan ya sanya ta zama wata ta daban........koda cikin mata dubu nawa zata shiga zaka hangeta ta fita daban a cikinsu. Glowing dinta,qyallinta da kyan fatarta daya cakuda da wannan sirritaccen kyan na asalin buzuwa ya sake zama wani abu na daban a gurinta,kwarjinin data debo daga jinin sultane shima ya qara zama ado a komai nata. Tsaf birra ta tayata ta shirya cikin wata sassauqar doguwar riga ta wani irin nau'in material da aka saqashi daga auduga da zare me daraja da tsada. Ko yaushe shirinta yakan zama me jan lokaci,tamkar shirin amaryar da ake kan hidimar aurar da ita,ahi yasa har yau har gobe tafiyarsu office dasu aisa bai taba zama daidai ba,har gwara ma lokacin dawowarsu. Sha biyu saura na rana,don haka ta qarasa dining room,buhaina ta ja mata kujera ta dora mata falin yanki ta zauna,sannan ta bara'atu ta matso tana dora mata wani yankin na musamman saman jikinta don kada wani sashe na jikinta ya baci,a lokacin tana duba kiran da yake shigowa wayarta. Daya daga cikin directors dinta na kamfani ne,saidai a yanzun bata cikin mode na wani magana daya shafi kamfanin,tana jiran ta gama settling wannan issue din dake gabanta tukunna,don haka ta maida wayar ta kife tana miqa hannu ta karbi spoon din da bara'atun keta miqo mata. Sama sama ta taba breakfast din,so samu tayi zamanta a kebantaccen balcony dinta,to amma kuma nannie ce.......tun jiya tasan da dawowarta,ta kuma aiko still an shaida mata,amma ta gaza zuwa,wata fuskar ai tafi gaban mari. Kawai dai bataso ta yiwa zuciyarta fami ne,tasan kuma halin nannie qwarai,bata tsoron ta mutu balle tayi rai muddin akan gaskiya ne. Sultane yana matuqar ji da ita,ita kadai ta rage masa cikin 'yan uwanshi hudi da yake dasu,su kadai suka rage a raye a duniya......don haka dukkaninsu da idanun matsayi irin na sultane suke kallonta. Miqewarta kawai ya gayawa birra me take nufi,don haka da sassarfa ta koma ciki,ta kuma dauko mata sassauqar alkyabbar da bata da wani nauyi ta daidaita mata ita saman kafadunta,sai tafara takawa kawai idanunta akan wayarta ba tare da tace komai kota dubi kowa ba. Yau din a cikin jininta takejin izza da kuma miskilancinta yana motsawa,don haka duk inda zata wuce,dukkan wanda Allah yayi yaga gilmawarta zubewa yake yana kwasar gaisuwa,duk kuwa da cewa basa samun damar ganin fuskarta,bara'atu da birra dake biye da ita suke amsa musu da sautin GODIYA TAKE. Daidai lokacin da aisa ke cikin katafaren parlour din nannie din,wani irin parlour da wanzuwarka ta farko a cikinsa zai gaya maka zallar sarautar da mamallakiyarsa take da jibi dashi. Bai cika kayan alatu ba,amma komai na cikinsa me daraja ne da janye hankali zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 55 ___________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah Dukkaninsu suna zaune a qasan tattausan carpet din saqar hannu dake mamaye da parlour din,aisan na kashingide gefan nannie din,dankwalin kanta a qasa,yayin da waya ke riqe a hannun nannie da alama amsa wayar takeyi. Sallamarta ta sanya dukkaninsu suka daga kai suna dubanta,aisa ce ta amsa tana tashi ta zauna sosai,suka hada idanu,sai akhnan din ta janye dubanta daga kan aisa din. Ko batayi magana ba ta gama fahimtar abinda akhnan ke nufi......fushin takeyi da gaske,haushinta takeji,to amma a irin wannan lokacin da idan ta hau wannan qadamin fahimtar da ita yake zama abu me wahala,sai itama ta share kaman bata fahimci me take nufi ba. A hankali ta tako zuwa gaban nannie a qasa kamar yadda ta samesu,ta zauna sosai tana tattare rigarta yadda zataji dadin zama,ta jingina da daya daga cikin kujerun alfarma da aka qawata parlour din,wanda sam sam basu ci guri ba. Qamshin daya motsa daga jikinta bayan zamanta ya sanya aisa dubanta. Ko bata tambayeta tasan daga gyaran jikinta na wata wata ta fito,duk kuwa da cewa ita din gwanar qamshi ce,bata tunanin akwai wani company na turare da suka qware wajen fidda nau'ikan turaruka masu tsada da kama jiki da basusan da zaman akhnan din ba,amma wannan qamshin nasu khumras da lab lab din incense by kabo daughter daban yake. Wani qamshi ne da zai dinga saukar miki da nishadi,kaji zuciyarka tana wani irin sanyi da saukar da cikakken nutsuwa. Har kullum kuma a koda yaushe,a duk kowanne wucewar daqiqa idan ta kalli akhnan mamaki take qara bata. Da gaske ne.....kamar yadda take fada,kamar kuma yadda ta saba fadi.....bata rasa komai ba.......Allah ya bata dukkan wata cika da siffa da kowacce diya mace zataso ta mallaka......Allah ya bata wasu irin qualities da kebantattun abubuwa masu yawan gaske.....a zahiri a iya abinda idanu ke gani bata da wani sauran naqasu ko buqata........amma ta kowace fuska da kowa ke iya hange mata tana da buqatuwa zuwa AURE......abu dayan nan da har yanzu bata gamsu da cewa haka yake ba. Har yau har kwanan gobe,har jiya da yanzu babu wani dalili guda daya da take basu ko zata basu kan haka,abinda kuma har a yanzun yake bawa aisa mamaki kenan da daure mata kai. Wannan dalilin guda daya bai kai mizani ba.....QASAITARTA DA IZZARTA da kuma surki na GIRMAN KAI a wasu lokuta,basu gaya mata daidai din cewa......su kadai sun isa su mallake su kuma mamaye gami da ci gaba da riqe mata rayuwa ba har izuwa ga bigiren da ya dace da ita. Hankalinta yana a kan waya,amma kunnuwanta na wajen nannie. Sai data zauna din sosai sannan ta fuskanci da HAIRAAN take wayar. Sau da dama takan manta da hairaan din shaf cikin mutanen dake existing a rayuwarsu. Tana mantawa da ita kwata kwata cikin babin rayuwarsu. Duk da kasancewar hairan din mutum me wani irin zuciyar zumunci......son duk mutumin daya rabi rayuwarta,da kuma girmama babba,wannan yayi sanadin da ta maida nannie qanwar mahaifinta kuma kaka a wajen ta ta halak malak. Idan hairaan tana nan,ba zaka taba banbance wata haifa ba tsakanin aisa da ita,idan hairaan tana nan,zaiyi wahala ka dauka morsa safiyya ce mamanta ba nannie ba,idan kaga sabanin hakan,nannie din bata nan ko kuma tayi wani balaguro. "To Allah ya kaimu......ya nuna mana cikin amincinsa da yardarsa......ma sha Allah......ga biftu" Ta fada tana miqawa akhnan wayar kai tsaye. Wani abu ne da batayi tsammaninsa ba,ba wani magana ko waya suke da Tante ba(kamar yadda falaak ke kiranta dashi),duk da hairaan din tana da wani irin kirki da jan 'yan uwanta a jikinta. Ko yaushe fuskarta shimfide take da fara'a,kamar yadda lokaci lokaci takan duban akhnan din koda ta watsapp ne,ita dince bata damu da duba hakan ba. Idan ta nemeta shikenan,idan bata nemeta ba koda tsahon shekaru nawa ne ita din bame damuwa ta nemeta bace. "Biftu na" Hairaan din ta fadi da salon kirkinta da kulawarta kwatankwacin wadda take nunawa falaak,saidai har yanzun ita din ta kasa jin haka har zuciyarta. Kamanni da kuma murya na hairaan dukkaninsu ta debo na morsa safiyya ne,wannan dalilin ya sanya kowanne qoqari na kawo kusanci tsakaninsu yake wargajewa a zuciyar akhnan. "Bonjour" Ta fada a taqaice da muryarta da tayi wani sanyi a yau da yake nuna batason magana. "Bonjour,comment ça va?" Ta maidata mata muryarta cike da nishadi. "Alhamdulillah" Ta sake amsa mata bata wani jin armashi a gaisuwar. "Fatan komai lafiya......ya sahel couture" "Alhmdlh" Ta sake amsa mata,don tana jin bata da amsar data wuce wannan. "Allah yayi jagora........muna kusa da zuwa gida in sha Allah,kafin qarshen shekarar nan". Idanunta ta lumshe ta kuma budesu,tana jin bata da wani hadi sam da wannan labarin. "C'est bon" Ta sake fadi a taqaice. "Ma sha Allah,Nous nous reparlerons bientôt in sha Allah(zamu sake magana nan kusa in sha Allah). Zare wayar tayi kawai daga kunnenta tana ajiyeta kuda Nannie. A nutse nannie ta kalleta tana qoqarin karantarta,sai ta janye idanunta,cikin nutsuwar nan dake cakude da qasaita tace. "Barka da warhaka......" Sai da nannie din ta gyara zamanta,tana kuma karantar yanayin boyayyar damuwa qasan ran akhnan din sannan ta amsa. "Barkanki dai......." "An dawo lafiya?,Allah ya karbi ibada" "Ameen summa ameen" Nannie ta amsa can qasan ranta cike fal da maganganu,saidai yanayin da take karanta tattare da akhnan din yana nuna mata abubuwa da yawa. Da yawan yawan abubuwan da take karanta din mamaki suke bata. Wanne irin mugun tunani ne a ranta har haka da fidda mijin aure yake zame mata babban abun tashin hankali ko kuma damuwa a tattare da ita?. "Abubuwa da yawa sun faru sanda bana nan biftu.......mene damuwarki ne?,akwai wani abu ne daya kamata a sani wanda baki fadeshi ba a zahiri?" Ta furta da sigar lallashi,tana tunanin ta wannan hanyar zata samu kamo bakin zaren damuwar akhnan din. Blue eyes din nan nata ta juya kadan tana janyesu cikin jin gajiya da yi mata maganar kowanne d'a namiji. Tana ganin basu kai matsayin da rayuwarta zata fuskanci takura irin wannan har haka ba......tana da 'yancin da zatayi rayuwarta ita kadai,don bataga ta inda hakan ya sabawa addini ba muddin tana da qarfin zuciya dana gwiwar rayuwa ita daya. "Ina saurarenki" Nannie ta sake fada tana bata dukka hankalinta. Tsam aisa ta miqe da zummar basu guri,amma sai Nannie din ta zube mata idanunta. "Dawo ki zauna......kunfi kusa da ita akan kowa,qilan akwai wani abun da bamu san dashi ba,ku zaku fimu sani......qilan akwai wani abun da ita ba zata iya fada ba,ku zaku fada" Tayi maganar cikin maida hankalin nan nata akan komai. Wuya ta karyar tana duban Nannie din,idanunta na nuna dukka gajiyawarta. "Nannie.......dama dai baki sani a wannan batun ba,don Allah kice na tafi" Ta fada tana burin hakan,don daga ita har shehnaz bata tunanin akwai wanda ya yiwa akhnan fahimta ta haqiqa akan wadannan tsare tsare nata. "Aisa!.....zama nace kiyi" Nannie ta fada da yanayin daya tabbatarwa aisa bada wasa take ba,don haka ta koma ta zauna a hankali. "Ehmmn.......ina jinki biftu" Ta sake maida tambayarta kan akhnan tana tsareta da kallonta. A nutse ta juya kanta,tana jin tuhumar Nannie takai mata ko ina. Koda ta fada fadin baida wani amfani,don bata zaton akwai ranar da zatazo su fahimci juna ita dasu. "Nannie......bana buqata......ana aure ne idan ana buqatarsa,iya rayuwata a haka ta gamsar dani Nannie ku fahimci haka......aure baya burgeni,koda nace zanyin zai zamana tawaya ce kawai ga martabata da mutuncina........bada umarni da karba........" "Ungo nan" Nannie ta furta cikin tsananin mamakin maganganun bakin akhnan da manufofinta da har yanzu basu canza ba. "Biftu?......khadeeja?,hankalinki guda kuwa?" Manyan idanunta ta lumshe,cikin ranta tana jin sassaucin da ba wani hadimi ko daya a gurin da Nannie tayi mata haka,ta san kadan daga aikinta,yin hakan gaban hadimanta bazai zame mata wani abu me wahala ba. "Aure cikar kimar maca ce ko kinqi ko kinso,duk wata daraja da martabatar d'iya mace ta ta'allaqa ne kan aurenta,shine mutuncinta,ko gawar me aure da maras shi sun banbamta gun daraja......" A hankali aisa ta sanya fuskarta tsakanin siririn mayafin kanta. Yau akhnan ta ja musu,bawai iya kanta kawai ba,harsu tasan yau Nannie saita tayar da dukkan wani tsohon ballinta a kansu. (08187255872 lu'u lu'u paying) "Me yake daurarki ne biftu?......me kike tunani?" Ta sake maimaitawa tana dan fidda idanunta akan akhnan nan. Kasa amsawa Nannie tayi,don zuwa yanzu maganganunta sun fara juyewa suna mata kama da maganganun morsa safiyya,dukkan alamu kuma suna nuna akwai wani qaqqarfan connection a tsakaninsu. Hakan bazai bata mamaki ba,tasan cewa komai matar zata iyayi don shiga tsakaninta da duk kowa da zai nuna so qauna ko kulawa a kanta.......takun me martaba kaf ya isheta mizanin da zata dora girman qiyayyar da morsa safiyyan take mata,da wannan mammina keson ta karbeta da irin karbar da ta yiwa mammina?......ta bata matsayin data bawa mammina?.......ta dorata daidai da mizanin data dora mammina akai?.....bata jin abune da zai yuwu sam.....har gaba da abada ba zata daina lasaftata a mazaunin manyan abokan adawarta ba......har abada ba zata daina irgata ba a mazaunin halittar da bata qaunar farincikinta ko walwalarta ba. Idanunta kawai ta maida ta lumshe tana jin saukar maganganu da fada daga bakin Nannie din irin wanda bai taba shiga tsakaninsu ba. Nannie din ta sani.......akhnan ba zata tanka ba,ba kuma zata ce komai ba,da wannan miskilancin.......da wannan izzar dake a cikin jininta ta barta ga gama fadanta yadda takeso. Nannie din daban take,tana kuma cikin mutane hudu rak a duniya da suka isa suyi mata fada,suna cikin mutane hudu rak da suka isa su daga mata yatsa ta kuma kalla,shi yasa ta zabi yin shuru a fuskar Nannie din. Tsam ta miqe tana tattara rigar jikinta dake a bude sosai daga qasa,sai Nannie ta daga kanta a nutse tana dubanta. Batakai ga yin magana ba YAABI daya daga cikin manyan hadimanta ta rangado sallama da muryarta dake da wani irin kaifin sauti. Hankulansu dukka ya koma ta gurin sanda take shigowa cike da qanqan da kai zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 56 ____________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah ____________________________ "Allah ya baki yawan rai.........giwa tana neman izinin shigowa gareki". Kalmar giwa ba baquwa bace ga kunnuwan dukka ahalin gidan sarautar agadez......mace daya tak ke da wannan sunan......ita kadai ce mamallakiyarsa wato ZAITUNA(MAMMINA). "Tana iya qarasowa" Ta fadi hakan ya baiwa yaabi daman juyawa da sassarfa tana jin wani banbarakwai na tsaiwar da mammina din tayi tun daga shingen farko tana neman izinin qarasowa. A hankali akhnan ta koma ta zauna,sai Nannie ta bita da kallo. "Kin fasa tafiya?,saboda kinji uwarki zata shigo kenan" Ta fadi cikin rashin bawa maganar muhimmanci tana laluben inda ta ajiye tasbaharta. Luf tayi da salon shariyarta,kamar bataji abinda Nannie din tace ba. Sai da aka zube kwanduna guda goma cass wanda hadiman mammina dana Nannie sukayi hidimar shigowa dasu sannan sallamarta ta karade parlor din. Ita kadai ke shigowa ciki,duk da tarin hadimanta ba mutum daya data bari ya shigo,koda kuwa yalwa. Fuskarta shimfide da wani lallausan murmushi take takowa zuwa cikin parlor din. Cikin cikakken ado take,wanda yake bayyana tsantsar dacewar sunan da ita wato GIWA. Wani irin yadi ne me alfarma da asalin tsada dan asalin qasar turkey da aka yiwa adon da ba jikin kowacce basarakiya zaka ganshi ba. Daga mayafin jikinta har qawatacciyar lallausan socks din qafarta data lullube ainihin qafarta daban suke. "Wa'alaikumussalam......maraba" Nannie ta fadi sanda mammina ke qarasowa parlor din. A hankali ta sulale a qasan carpet din,cikin tsananin ban girma,fuskarta kwance da murmushi ta soma fadin "Ayimin afuwa......bani da kowanne labari na dawowarki Nannie,sai da asubahin yau......jiya na yini cikin hidimar masu bukukuwan aure......sai can dare na samu kaina......da asubahin yau din kuma yayi wuri a tasheki". Qaramin murmushi Nannie ta saki. "Hidima bata qare miki zaituna,tunda ban ganki ba nasan akwai abinda ya faru,amma safiyya tasa anyi komai daya dace.......ina fatan na sameku lafiya". A hankali ta hadiye wani abu,ta kuma ci gaba da tabbatar da fuskarta a yanayin da take. "Komai lafiya alhamdulillah" "Ma sha Allah" Ta fada tana jinjina kai. "Ga kayan barka da sauka nan,ina fata basuzo a makare ba" Mammina ta fadi tana dan rusunar da kanta. Wajen Nannie ta waiwaya ta kalla tana murmushi,batasan me yasa kirkin mammina yake neman yayi yawa ba,bata gajiya da hidimarta da hidimar duk wanda ya jibanci sultane. "Wannan kayan ba iya ni fatimatou kawai ba......harda dukkan wani wanda yake qarqashin bangaren fatimatou ne......kin kawo sanda wadannan 'yan buruntun suke kusa" Ta fadi tana nuna aisa da baki. Waiwayawa tayi yana murmushi ta dubi aisa,tunda safen aisa ta shiga sun gaisa ita shehnaz,saidai akwai wani dan abu data karanta dangane da mode din yaran. Ta nazarcesu tsaf,dukkan abinda ta hanga din kaifin idanu dana zuciyarta ne suka tsinko mata shi,amma sam su kansu basu sanya shi a mizanin da yanayin yadda idanuwa zasu iya gani ba. Kaifin ganinta da tsinkayenta ya zarta yadda mutum zaiyi hasashe,ita kanta tasan wannan yana cikin baiwarwakinta da take alfahari dasu,tasan kuma suna cikin abubuwan da suka tabbatar da nasarar rayuwarta a matakin da take kai yanzu. Murmushi ta sakarwa aisa din kamar yadda itama ta sakar Mata,sai mammina din ta maida dubanta kan Nannie. "Mammina" Akhnan ta fada da wani irin yanayi dake nuna zallar sakewa daya sake fidda quruciyarta,ya sake daukan shekarunta kuma ya maida can baya,zamanin da quruciyar zalla ke cikin jikinta sosai,saita matsa zuwa jikin mammina din sosai ta zauna. Hannuta mammina ta riqo tana dubanta. "Na biya ta sashenki,kamar bakici abinci da safennan ba yadda ya kamata,me ya hana hakan biftu?" Ta fada a tausashe tana duban idanunta cikin nuna zallar kulawa. "Biftu din dake dosar shekaru ashirin da biyar akewa haka.......zaituna kam bansan sai yaushe zaki daina kallon khadeeja har yanzu a mizanin yarinya ba" Nannie ta fadi tana dubansu da kyau. Murmushi ta danyi,saidai kuma cikin nata kakkaifan hangen.....cikin nazarin nan nata takeji a jikinta ya kamata ta fara magana,ita ya kamata ta fara cewa wani abu ba Nannie ba......akwai wani harsashin daya kamata ta kafashi a irin wannan gurin,a irin wannan lokacin,don haka tayi qasa da kanta kadan. "Nace ba......idan ba damuwa,idan kuma da lokacin da za'a iya bani,inaso muyi magana". A nutse Nannie ke dubanta,yadda zaituna ke bata girma yana kamanceceniya da yadda take bawa sultane. Bata dubanta sam a mazaunin qanwar MIJI girma take bata irin na YAYAR MIJI. "Ba wani lokaci da ba zaki sameshi ba zaituna.......bismillah" Tayi maganar daidai sanda aisa ta miqe a karo na biyu,sai itama akhnan ta yunqura zata miqe "Zauna......maganan ke ya shafa kai tsaye" Yadda sautin ya fita daga bakin mammina din ya sanya akhnan daga kai tadan kalleta. Akwai dan kaurarawa kadan cikin muryar mammina din,ba kamar lokutan data saba yin magana da ita ba. "Gata nan Nannie......kiyi mata fada ko ke zataji naki" Mammina ta fada cikin wata sassanyar murya gami da yin qasa da kanta. Duban akhnan Nannie tayi,kaman yadda akhnan ta daga kai ta dubeta itama. Tsahon wasu sakanni sannan kowa ya dauke kallonsa daga kan dan uwansa. "Yau kuma?......ni fatimatou?,qarar biftu?" Nannie ta fadi cikin mamakin daya kasa bayyanuwa hatta a saman fuskarta. Kai mammina ta girgiza tana duban Nannie a nutse. "Kamawa takeyi Nannie.......yau ta kama na kawo miki qararta.......saboda tana neman hana zaman lafiya tsakanina da morsa safiyya". Iya furta sunan morsa safiyyan kadai ya qarawa akhnan zafi a zuciyarta. Taja wani numfashi tana qoqarin calming kanta. Girman matsalolin morsa safiyya cikin rayuwarta har yakai mammina ta kawo qararta saboda ita?,abinda bata taba aikatawa ba?. "Ina jinki" Nannie ta fadi tana gyara zamanta gami da sake tattara hankalinta akan mammina. "Nannie.......komai da akhnan zatayi koda bada sanin zaituna ba morsa safiyya na azashi akan mizanin NICE SILA.....nike da alhakin yin komai da akhnan zatayi ko tayi.......dukkan iya bakin qoqarina wajen samar da kyakkyawar alaqa da kuma fahimtar juna ina yinsa,ina qarar da dukka qarfina da tunanina wajen ganin akhnan ta fahimci girman alaqar dake tsakaninta da morsa........amma duk yadda nakai ga nuna mata hakan wasu lokutan sai tayi burus,inda a take kuma morsa safiyya ke aza alhakin hakan a kaina......kaman matsalolin dake faruwa kwana kwanan nan.......duk duniya bani da mafita a idanun morsa safiyya......kwana da wuni nake wajen bata lokacin fahimtar da akhnan muhimmancin bin umarnin sultane......darajar kowacce mace gidan aure kaman yadda aure ne itama ya haifeta,saidai na gaya mata ina tsaginta......ina kuma bayanta,bazan mara baya ayi mata auren dole ko aure da wanda bai cancanta ba......amma fidda miji da cika umarnin sultane ya zama wajibi a kanta......ki tayani fahimtar da ita don Allah Nannie......inaso mu zauna lafiya da morsa safiyya.......inaso muyi zama na zumunci da qaunar juna da ita.......amma na gagara samun hakan tsahon shekaru ashirin ina abu daya!" Ta qarashe maganar cikin sautin muryarta yana nuna wani abu ya taba rai da zuciyarta sosai da gasken gaske. Dakatawa tayi tana maida numfashi,idanunta yana wani irin narai narai kaman hawaye ne kwance a cikinsu. "Inaso mu zauna lafiya......inason ta fahimce ni,inaso ta gane cewa inason jininsu har zuciyata......ba laifina bane kome daya faru,tsarin Allah ne,kaman yadda na dauki tawa qaddarar a baya,daga baya Allah yayi ikonsa....ya kamata itama ta fahimci hakan,ta yarda da hakan,mu rayu cikin aminci da salama,mu samawa sultane nutsuwa a mulkinsa ta hanyar hada kawunanmu guri daya......na gaza fahimtar da ita hakan" Ta qarasa fada tana yin qasa da kanta da wani irin rauni. Sosai abun ya taba ran Nannie,iya zamanta da mammina a duka shekarun nan ba zata ce ga wani halinta mara kyau guda daya ba.......ba zata ce ga wani abu guda daya mummuna da taba taba tsinkaya daga gurinta ba. Ko abubuwan da suka shude a shekarun baya.....a shekarun da dukkaninsu quruciya ke zagaya a jininsu ta jingina hakan da sabanin fahimta da aka samu akan mammina zaituna din......wanda daga baya ta wanke dukkan komai daga zuciyar kowa.....har kawo yau kuma ba wani me mummunar shaida ko abun ala wadai a kanta. Zuciyar Nannie tayi rauni,tausayin mammina ya kamata,kaman yadda akhnan taji zuciyarta tana tafasa akan hawayen data gani yana shirin zuba da idanun mammina din. Ta kasa jurewa da wannan gajeran haqurin nata.......ta gaza danne wannan zuciyartata da fushi ke yawan mata tasiri,ta matsa baya tana jingina da kujera cikin bacin rai. "Da wannan kalar bacin ran da take dasa mata?.....da wannan kalar dabi'un nata?,ta yaya zanji qaunarta a zuciyata?......ta yaya?.....har abada Nannie.....karkice zakice wani abu dani,taci gaba da amsa wannan sunan,taci gaba da riqe wannan sunan,amma ba zata taba samun komai daga gurina ba,sai wannan tursasawar kadai da zata yita ganinta a idanu na da ayyukana" Tana kaiwa nan ta miqe tana tattare rigarta. "Kada kice na zauna Nannie......tafiya zanyi" "Dole ki zauna akhnan......" Nannie ta fada a kausashe. Blue eyes dinta ta daga ta zubawa Nannie,sai dukka kamanninta da sultane suka sake fita baro baro,take taji kamar da sultane take magana,don haka ta sulale a nutse tana jin zuciyarta kamar zata fashe. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Ko baki gyara batacciyar alaqar dake tsakanin mammina da morsa ba......dole ki karbi baqonki na yau da mutunci da karramawa......baqonki na yau daidai yake da mutuncin sultane......daidai yake da martabar mammina......daidai yake da kima ta ni fatimatou hammud!". Har tsakiyar kanta taji saukar maganganun Nannie. "Waye wannan?" Ta tambayi kanta da wani irin hautsinannen yanayi. Waye wannan da a yau yake karbar kakkausar kashedi data jima bata ji irinsa ba kaf cikin rayuwarta a kansa?. Duka sauran abinda Nannie ke fadi ma bata ji ba bare ta fahimta,ta miqe kawai a hankali tana takawa ta fita a sassan zuwa sassanta kai tsaye. Tun a gate na biyu na sassanta ta shaida birra bata buqatar kowa kusa da inda take,tun daga nan bata baiwa kowa damar wanzuwa a gurin ba ballantana akai ga qofar da zata sadaka da kashi kashin faluka da dakunan hutawarta har yakai ga bedroom dinta da yake number na uku cikin dakunan baccinta. Takan jima bata shiga dakin ba,saboda yawan zamanta a Niamey daya rinjayi adadin zamanta a nan agadez. Takai ta kawo har batasan adadi ba,tunaninta yana sake tsere da son kamo wani abu. Daga yadda Nannie ke magana a kansa.......daga yadda Nannie ke maimaita mata batunsa tabbas akwai wani abu.....wani abu da zataso ta fuskanta komai qanqantarsa. Abu guda ta sani.......a yanzu,a wannan lokacin bata shirya auren kowanne d'a namiji ba bare ya sanya rai zata rayu qasan dokokinsa da kuna juyawarsa akan al'amuranta cikin kowanne yanayi da yaso. Shawara ta sauya,ta jawo wayar dake dakin wadda ke bata daman kiran kowanne sashe na sassan gidan nata dama sauran sassansu mammina. Wadda take buqata ita ta fara daukan wayar wato birra. "Ki qaraso ciki yanzun nan" Ta furta tana maida wayar ta ajiye,sannan ta miqe tana rage tazarar nisan da tayi da falukan nata. "Tashi" Akhnan tace da birra kai tsaye a sanda birra din ke shirin rusuna mata. Duk da cewa ta miqe din amma ta kasa tsaiwa sosai,don tana ganin kamar zata hada tsahonta ne dana akhnan. "Ki zabi mutum shida......inason su sanya min idanu cikin masarautar agadez da kewayenta,komai qanqantar labari daga baqon yau da zaizo gurina ina da buqatarsa,ina buqatar kowanne bayani daya shafeshi" Ta fadi ba tare da tako dubi birra ba. Kanta ta qasqantar,tana jin girman aikin da akhnan din ta bata. Tasan wasu abubuwa game dashi din,saboda dukkan yanayi yana alamta cewa wannan baqon yasha banban da sauran baqin da takeyi din. Har tayi taku uku ta dakata,tana tuna cewa birra batace komai ba akan maganganunta,koda kalmar TO data saba cewa a duk sanda tayi umarni da wani abu. "Kamar kinsan wani abu da yake ni bansan dashi ba.......meye wannan abun?" Ta jefawa birra tambayar tana waiwayowa gami da zube mata kyawawan blue eyes dinta. Qasa birra tayi da kanta,aminci ne zalla a tsakaninsu tsahon shekarun da suka diba suna hidimta mata,alqawari ne da kuma rantsuwa sukayi akan ba zasu taba cutar da ita ba sam sam......amana da sirri sune zasu wanzu a tsakaninsu har abada,komai tsanani. A sanyaye ta motsa labbanta zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 57 ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ____________________________ "Morsa safiyya ce ta karbi ragamar shirin tarbarsa". Sosai ta zubawa birra idanu tana qoqarin hado bakin zaren maganar tata. Morsa safiyya?......a hannu cikin shirin zuwan baqo gareta?. "Indai har a wannan karon morsa safiyya keda hidimar tarbarsa......tabbas ya riga daya fadi.......ya kuma rasata tun kafin ya sanya qafafunsa masarautar agadez" Ta raya hakan a zuciyarta tana gyada kanta gami da jin wani abu yana tasiri a ranta. "Daga wanne yanki zaizo?" Ta sake tambayar birra tana jin kwanciyar hankali a ranta. "Zinder......daga zinder ne uwar gijiyata". "Jeki......iya haka kawai ya wadatar" Ta fada tana sake samun sukuni cikin ranta. Koda morsa safiyya bata da alaqa da zuwansa......koda bata da alaqa dashi,amma akwai wani abu a tare dashi da tayi liking,har takejin ya cancanci wannan tarbar irin tata. Wani qasaitaccen murmushi ya subuce mata......wataqila tarin addu'o'inta ne a yau Allah zai amsa mata......tarin fatanta ne yau qila zai cika......koda a iya wannan ranar......koda a iya wannan lokacin kadai ta nunawa morsa safiyya iyakarta ita ya wadatar da ita......ko yaya tanason ta gwada mata batakai ba,wataqila hakan ya zama silar da zata fita a rayuwarta,ta kuma nesanta kanta da dukka abinda ya shafeta kamar yadda ta jima tana buri da kuma muradi. "Kayi kuskure" Ta fada qasa qasa tana hayewa saman qasaitaccen gadon da aka kashema lokaci da kudi kafin wanzuwarsa a dakin. Ta lume sosai cikin duvet da comforter tana lumshe idanunta. Tana wassafa irin sallamar da zatayi masa......tana wassafa irin bankwanar da zasuyi dashi.......irin bankwanar da zata zamewa duk wani me gigin sake zuwa gareta izinar da bazai kuma sha'awar ganawa da ita ba bare ya buraci ta zama MATARSA!. "wai mata?" Ta sake maimaita kalmar a fili tana sake maida idanunta ta lumshesu. Tana sake cika da mamakin tsaurin ido iri na maza.......tana same tariyo wadanda suka taba zuwa gurinta. Mutum daidai har goma sha uku. Dukkaninsu babu wani qasqantaccen mutum........babu wani me muni ko talaka a cikin su,hasalima su da iyayensu dukka sannanu kuma manyan mutanene tsakanin qasar niger din,Nigeria,Gabon,Camaro,Chad harma da algeria da kuma Egypt. Sai YANAAR da yayi tattaki tun daga Istanbul. Wani siririn tsaki taja,haushi yana sake cikata. Waisu dukkaninsu gani sukeyi suna da wani quality isa ko qarfin kaiwa da zasu mallaketa?. A nasu yaudarar kawunansu,sun cika nauyin mizani da ma'aunin aure da mallakar akhnan?. Wani murmushi ta saki tana aza kanta sosai saman pillow,tana jin adadin yaudarar kawunansu dake tattare dasu,zallar wauta da kuma wawantar da kansu. Hankalinta a yanzun a kwance yake ba kamar dazu ba,lokaci kawai take jira,shi yasa takejin baccin da batayi jiya ba isashe a yanzun yana kama idanunta,tana jin gwara tayi baccin ta sake tashi fresh. Har saman kanta taja comforter din ta rufe,lallausan qamshin jikinta da wanda yake fita daga shimfidun alfarma na gadon suka hadu suka gauraya,suka bada wani kalar qamshi me wani irin sanyi tare da nuna ajin mamallakin dukka wannan qamshin. *FALAAK* A nutse take fitowa a dakinta tana kuma takowa zuwa ainihin parlor din morsa na musamman da take hutawa. Sakakkiyar doguwar riga 'yar turkey ce a jikinta da mayafinta dukka da suka kasance kalar olive green. Littafine dan qarami a hannunta data manneshi a qirjinta,idanunta akan morsa dake kashingide sanda take takowar,sai badee'a dake tsugunne a gafenta,kusa da ita wata kyakkyawar leda ce a ciki da ta tabbatar hijabanta ne a ciki. Dab da zata qaraso morsa safiyya ta daga kai tana qare mata kallo. Daga jiya zuwa yau tana gani wani baqon yanayi tattare da falaak din. Ba zatace ga irin yanayin ba,ko kuma ga abinda ya faru,saidai tasan akwai wani baqon abu tattare da ita. Da farko ta dauko ko daga malamin ne,amma kuma yadda ta zauna tana mata bayanin gamsuwar da tayi da Sheikh haisam sama da oustaz Ousmane sai hankalinta ya kwanta. "Da gaske na dabanne momma........har yanxu na kasa aminta wai koyarwa yakeyi momma.......". "Me yasa kika ce haka?" Kai falaak ta jinjina idanunta kan abincin gabanta da take juyawa da cokali. "Ban taba ganin sheikh irinsa ba momma.........wani irin izza nake hange a jininsa,yafimin kama da jinin sarauta ko basarake" Ta qarasa maganar tana sauke idanunta akan momma. Idanu momma din ta zuba mata,sai kuma ta janye dubanta tana son gano wannan yabon da falaak ke masa na kusan mintina talatin,to amma saita tuna,ko sultane sai daya kirata ya masa maganarsa,ya kuma tabbatar mata ya gamsu dashi dari bisa dari. Har sultane din yaso bata dariya sanda yace. "So samu ko sau daya a sati mu dinga zama dashi yana karantar dani safiyya" Murmushi me kama da dariya ta saki. "Sultane guda?,kuma ina kaga lokacin?". Ta fadi duk da tasan halinsa. Mutum ne me sauqin kai idan ka fahimceshi,hakanan ma'abocin son karatuttukan addini ne. Sau da dama idan ya kebe baya komai,zaka sameshi yana sauraren karatuttukan malam da ya aminta da koyarwarsu ne. Yakance. "Muna mulki ne kawai don ya zama dole a kanmu,amna shugabanci masifa ce da saidai mu roqi Allah ya fiddamu ranar qiyama,duk yadda mukakai ga kwatanta adalci kuwa.......rayuwa duniya ba komai a cikin ta safiyya face rudu,idan baka nema ilimi ba.....duk girman rawaninka ba ruwan Allah da wannan,ranar qiyama zai saita hanyarka zuwa wuta" To ko a yanzun ma murmushi shima ya maida mata. "Safiyya......ilimi kogi ne,ta inda ka qare ta nan wani ya fara......na hangi wata irin nutsuwa a tare dashi,da wani irin hasken ilimi,zai wahala nan gaba kadan ban shugabantar dashi ba,inaji a jikina na samu wani mashawarci na kusa kusa da bani dashi sanadin rashin haihuwar d'a namiji". Dukka bayanansu shida falaak itama ya sake saka mata nutsuwa dashi,duk da cewa bata samu ganawa dashi ba a ranar,don kafin ta fito har ya wuce bayan ya sallami su falaak. "Ba asalin dan qasar nan bane,ba wani bane kuma,almajiri ne mai tarin ilimin addini,kawai kinsan ilimin addini yana sawa mutum wani irin kwarjini ne.........to amma alhamdulillah......dama abinda ake gudu a samu qasa da wanda ya kai oustaz Ousmane din" Kai falaak ta jinjina. "Amma da gaske yana da doka momma......yace dole saidai na samu me rakani karatun,ko mu dauka tare,ko ta zauna ta jira a kammala qaramin". "Ba damuwa bane......ga badi'a" "Nima itace tazo raina" Falaak ta fadi tana diban abincin takai bakinta. A gefe ta ajiye littafin tana hawa saman babbar daddumar da momma ke kashingide akai. "Allah yasa manya ne hijaban badi'a". "Manyan kike sha'awa kuma?" Momma ta fada tana juya wani dan qaramin akwati a hannunta wanda ke dauke da wata irin azurfa me daraja da aka sarrafata daga turkey. "Haka yace......sheikh haisam ne yace shi zan dinga sakawa" Ta furta idanunta akan hijaban da badi'a ta zazzage tana daga mata su. Murmushi ya qwacewa falaak,ta hade hannunta guri daya. "Wanne irin jilbab ne haka masu kyau badi'a?". "Huguma closet.......can na shiga na dubasu......yanzun nan sarkin gida ya aika aka karbosu,har qofar gida daga garejin mota suka bayar takanas aka kawo". Kai falaak ta jinjina,bata sake ma cewa komai ba don tasan irin kayan da huguma closet din suke saidawa. Wani irin quality garesu,price din su kullum mamaki yake bata. Tana hira wani lokaci da hadimanta da sukan shiga Nigeria siyayya,sun sha gaya mata ko cikin kano ba kowanne kasuwa da shago bane yake da irin nata price din ba. 08187255862 Join our WhatsApp group. https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX (Muna aika kaya ko ina cikin Nigeria,nijer,ghana da Cameron). "Ki kaimin ciki badi'a,saura awa biyu lokacin shiga aji yayi" "An gama ranki ya dade". Ta fadi ta yunqura tana kwashe kayan. Barin badi'a gurin morsa ta ajiye akwatin zoben hannunta. Ta dubi falaak,har qasan ranta tana jin dadin yadda karatu ya kama zuciyar falaak din,inama ace hakan zata faru da akhnan ko sau daya ne?. "Momma.......don Allah ba gulma ba" Falaak ta fada tana murmushi. Itama qaramin murmushin ta saka. "Gulma mana falaak" Murmushi tayi sosai,har sai da jerarrun haqoranta suka bayyana. "Allah ba gulma ba kawai inason sani". " Fadi falaak" Morsa ta fada tana kallon agogon dake daura dasu. "Don Allah wanne kalan baqo wannan karon yaa akhnan zatayi......ina fata ya zama shine miji na qarshe da zata zaba" Shuru kadan morsa din tayi,abinda yaja hankalin falaak ta zubawa morsa din idanu. Nisawa tayi a hankali,ta miqe ta zauna tana duban falaak. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Shine mijinta in sha Allah......miji me addini.......mijin da zai saita rayuwarta,ya fiddata daga duhu zuwa haske.....mijin da zatayi alfahari dashi duniya da lahira.......HAKEEM JALAAL". Idanu falaak ta waro kafin ta samu ta hadiye wani yawu,tana duban morsa kaman ba zata daina ba,kafin daga bisani ta tattaro qwarin gwiwarta tace. "Morsa......hakeem zinder?......hakeem din abba liman?" Kai morsa ta jinjina tana duban falaak cikin tsakiyar idanunta. Sai falaak din ta zare idonta tayi gefe dashi tana jinjina kai. "Bai dace da ita ba?.....ko bai cancanta ba?" Morsa tayiwa falaak tambayar da ajiyayyar manufarta. Tanason gwada mizanin hankalin falaak din,tanason kuma gano zurfin nata burin akan kalar nata mijin auren.......cikin fargaba da fatan kada zaqin sarauta ya sanya tabi sahun burika da zabukan 'yar uwarta. Da sauri ta maido dubanta ga morsa tana girgiza kai. "Ko kadan morsa......hakeem fa?,ba shine yake zuwa ma niger na daya a gasar karatun qur'ani ba shekara biyar a jere?.......ba shine wanda ya wakilci niger ba a gasar izu sittin da tafseer na duniya ba?......ko ba shine dalibin da yafi kowa hazaqa ba a shekarar daya bar jami'atu ummulquraa?" Kai morsa ke jinjinawa tana jin tashin hankalinta kan kokwanton bin sahun akhnan daga falaak yana raguwa. "Shine falaak" Sai data saki murmushi sannan tace. "Ya cancanta morsa.....wallahi yakai......Allah yasa yaa akhnan ta fahimci hakan. Akwai wata nutsuwa ta daban tattare da maza irinsa......" Sai kuma ta dakata da maganan ganin yadda morsa ta zuba mata ido. "Meye naki burin game da mijin aurenki?" Morsa safiyya ta samu kanta da tambayar falaak kai tsaye. Wani irin nauyi da kunyar morsa irin wadda bata taba ji ba ta saukowa falaak. Sai ta miqe kawai da dan saurinta tana qunshe dariya tana barin gurin da sauri sauri. Samun kanta tayi da kifewa saman gadonta,tambayar morsa na mata amsa kuwwa a kunne,sai ta tsinci kanta da tambayar kanta ta hanyar maimaita tambayar da morsa tayi mata yanzu yanzu. "Meye zabinki?....ko kuma burinki dangane da kalar mijin aure?" Ta maimaitawa kanta da kanta wannan tambayar,wadda ta taho ne gilmawar kamannin hakeem kafin cikin qiftawar ado ya kauce,hoton sheikh haisam ya maye gurbinsa. Wani matsanaciyar faduwa gabanta yayi,har tana jin sautin bugun zuciyarta cikin kunnenta,ta runtse idanunta da sauri tana jin kamar kowacce kafar jikinta na tsatstsafo mata da gumi. Da hanzari ta miqe ta zauna,ta laluba makunnin qwayayen dakin nata tana qara musu haske,don wani irin qara tsananta bugu zuciyarta keyi da duk gilmawar second da wanzuwar wannan tunanin cikin kwanya da idanunta. ★Cikin babbar saharar data kasance wani guri na debe kewa,wani guri na gudanar da bukukuwa ko kwanan al'ada daya zama wani abu da aka saba dashi cikin yarensu da qabilarsu ta buzaye. Filinne me cike da sahara.......saidai kuma wannan saharar wani irin farin rairayin yashine mai taushi,amma kuma duk da tsananin taushin nasa tana jin yadda take iya zabga gudu saman raqumin da yake tafiya da wani irin kuzari kamar yana raka tsandaurin qasa bawai yashi ba. Nishadi takeji sosai,raquminta.......yashin dama suturar jikinta dukkaninsu farare ne,sai wata irin iska me dadi dake kadata hankali kwance. Tsaiwa tayi saman raqumin maimakon zama saman bayansa saboda dadin gudun da yakeyi da ita,ta ware dukka hannayenta kamar me shirin kama iskar dake wuceta da wani irin gudu,saidai ba zato ba tsammani ta hangeshi yasha gabanta yana nashi gudun ba tare daya ko juyo ya kalleta ba. Jikinta a sanyaye ta zauna saman raqumin tana sake bashi qaimi don isa gareshi,ta kuma wuceshi.kamar yadda shima ya wuceta,tana gudun tana duban bayansa. Shiga yayi irin ta cikakken buzu,rawaninsa da wandon yadin jikinsa,saidai kuma maimakon yasa rigar kayan,fara qal din t.shirt ce a jikinsa. Tana gudun tana qara kusa dashi,amma still bai waiwayo ba bare ya duba ta kusa cimmasa,wannan farincikin ya sakata miqewa kaman dazu tana ware hannayenta,saidai a wannan karon sai taji an cafki hannun nata,abinda ya sanyata juyawa bangaren hagunta inda aka riqe mata hannun don ganin waye. Saman wani raqumi yake shima,fuskarsa nannade da baqin rawanin da bazaiyiwu ta fahimci waye ba,kwanyarta bata gama daidaituwa ba mutumin dake riqe da hannun nata ya wani finciketa,abinda ya sakata sakin wani razanannen ihu tana duban nisan dake tsakanin raqumin nata da qasa a razane,qarar kuma data sakashi cin wani irin birki ya juyo da raquminsa da akalarsa gaba daya yana tunkaro nata raqumin da kuma mutumin da har yanzu yake niyyar kaita qasa. Dab da zata isa ga qasa taji ya cafkota,shige yadda ya cafketa a wancan karon da thunder yake shirin kaita qasa. Duk da a razane take amma hakan bai hana haduwar idanunsu ba,wata irin iska ta taso zata yaye nadin dake tsakanin bakinsa da hancinsa. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 58 A hankali taja ana janye lullubin jikinta,wanda yayi kusan yi mata daidai da lullubin mayafin da tayi cikin filin sukuwar dawakan,abinda ya sanyata riqe mayafin da kyau,tayi wani juyi daya tilastata bude idanunta da sauri ba tare data shirya ba. Saman fuskar aisa suka sauka,aisar dake tsaye a kanta tana duban fuskarta cike da mamakin kalar wannan abun da takeyi cikin baccinta,wanda ta tabbatar da cewa ba komai bane mafarki ne. Maida idanunta tayi yana lumshesu,gabanta yana wani irin dokawa,zuciyarta na wani irin gudu tamkar yadda taji a sadda komai ya faru a zahiri. Wani matsanancin bacin rai ne taji yana saukar mata,haushin aisa da haushin kanta da kanta yana cikata. Don me yasa aisa zata tasheta a sanda take dab da ganin fuskarsa?,me yasa ita din bata kai hannunta ta yaye lullubin da hanzari ba kafin aisa takai ga tashinta?.......me yasa aisa zata mata haka?,fuskar data jima tanaso ta gani ko hakan zai taimaka mata wajen gane wayeshi?. "Ki tashi hakanan da wannan mafarkin naki........ko ba'a fadi ba wannan mafarkin ne daya zame miki jiki.......awa guda kacal ta rage baqonki ya qaraso inji mammina......ki tashi birra na jiranki". Blue eyes dinta ta bude a nutse,tana kuma watsasu saman fuskar aisa din. Muhimmancin mafarkin.......da kuma muhimmancin da ganin fuskarsa yake a wajenta yafi muhimmancin baqon da aisa din ke magana akai,inda aisa tasan muhimmancin abun a gurinta da bata soma tadata ba akan wani mutum can da tuni ta gama yi masa nasa kalar matsayin. A yanzu duk duniya bata jin tana da buri na biyun sanin wayeshi?......waye wannan daya bata dukkan wani record na rayuwarta,ya bata mata kyakkyawan tarihin da take dashi na tabbatuwar NASARA cikin kowanne taku motsi da gasa. Alwashi taci......sai kuma ta cikashi,ko waye shi sai ta bincikashi,sai ta yaye duvet din a hankali tana jan jikinta zuwa bakin gadon ta sauke qafafunta. "Kada ki dinga wani abu kamar kin damu dani......kamar kuma kin damu da halin da nake ciki" Akhnan ta fadi cikin nuna halin ko in kula,tana kuma qin duban koda sashen da aisa take ne. Idanu kadan aisa ta zuba mata,ta fahimci a birkice take,a kuma wannan yanayin da take ciki bata buqatar suyi rigima ko kadan. Ta karanci wani abu,duk sanda zai ziyarci mafarkinta,da dukkan zuciya da kuma feelings dinta takejin komai da zai faru a mafarkin kaman a gaske ne. Bata fiya daukan FADUWA ba.......amma kuma zuciyarta bata da riqo irin wannan. Kafiya da taurin kai tabbas wannan cikin halayenta ne,amma riqo kam idan ta sakashi a cikin dabi'unta tasan da gaske ta mata qazafi. "Biftu" Aisa ta kira sunanta,sai tayi kamar bata jita ba,ta qarasa gaban masaqalin da lausasan towel dinta ke a jere ta dauki dan madaidaicin ciki tana wucewa toilet. *HAISAM* Cikin nutsuwa ya zube dukka idanunsa saman system din gabansa,wadda a qalla kusan awa biyu ya kwashe a zaune din. Sun gama tattaunawa dasu beena,wanda kowannensu yake wani sashe na daban cikin niger din don baza komarsu yadda ya dace. A yanzu da hussam yake waya,wanda kusan duka tattaunawar akan kamfanin turarensa ne da a yanzun suka samu labarin fitar wani qamshi dake shige da nasu a kasuwa. Numfashi yaja yana lumshe kyawawan idanunsa masu yawan eye lashes,ya sakeyin relaxing yana ci gaba da duban hussam. Ya fara gajiya da wannan tarin complain din da tun dazun yaketa abu daya,baisan me yakeso ba kuma. "Hussam" Ya kirashi da wannan coolness din nasa. "Obbo.....Allah obbo ka..." "Ya isa.....,magananka yayi tsaho da yawa haka,da nazari nakeyi zuwa yanzu na karanta fuula(pages) masu yawa......maimakon hakan ka bata duka wannan lokacin mana wajen binciken sabon scent mana?" Ya qarasa maganar da sigar tambaya wanda kai tsaye hussam yasan umarni ne. Kai hussam din ya jinjina,yana nufin cewa wani abu sallamarta da muryarta ya sauka a kunnensa. Ci gaba da kallon screen din haisam yayi ba tare daya ware yatsunsa dake cikin na juna ba. A hankali taci gaba da takowa tana jin yadda sautin bugun zuciyarta yake qaruwa. Tunda ta iso dab da gurin taji sassanyar muryarsa na fita ta system din radau kaman yana a wajen. Wannan sautin da take kwana ta kuma tashi da kewarsa. Ba'a maganar kyakkyawar fuskarsa data mata wani irin nisan da ba wanda yasan me takeji?,ya kuma takeji?,daga ita sai Allahnta kawai. "Ani dagadheera saamee(na manta samee)" Hussam ya fadi yana waiwaya kadan ya dubeta,abinda ya bawa haisam daman hangota kenan. Kamar kullum cikin jilbab dinta da yake yawaita dacewa da fatarta da kuma doguwar fuskarta,ma'abociyar siririn hanci,sak kamannin kyawawan 'yammatan qabilar oromo. Kanta a qasa,saidai hakan ya qaryatata. Ga duk me zuzzurfa da dogon nazari irin haisam din,kai tsaye zai fuskanci hankalinta yana fusguwa ga son kallon screen din system din hussam din,saidai tana qoqarin hana kanta faruwar hakan. "Daqiiqaa tokko naaf kenni(bani minti daya),zamuyi sallama da captain obbo" Ya fadi tare da waiwayowa gaba daya yana duban haisam din. "Obbo......ina ganin zan siya ticket kawai,zan wuce addis ababa gobe da safen.....zamu tura wasu sample na hadin sabon scent zuwa china.......akwai yuwuwar na tafi china din da kaina,akwai yiwuwar mu tura". Kansa yake gyada masa a nutse,kafin yace. "Ka sallameta tukunna". Yayi maganar yana masa nuni da idanunsa "Obbo.....wani littafi take nema......ina zaton kuma saina masa duba me kyau,kalleta ka gani ba sauri take ba a zaune take" Yayi maganar yana juyar da fuskar system din inda saamee ke zaune. Idanunsa haisam din ya janye,daidai sanda ta daga kanta zuwa ga allon system din. Tana jin duk wata juriyarta ta qare,koda ta cikin allon computer din tana muradin ganin fuskarsa. "Nagaan waaree booda obbo(barka da yamma obbo)" Ta fada a hankali tana sauke idanunta akan fuskarsa. "Barka kade saamee......ya dalibai?" Yayi maganar yana qoqarin jawo wayarsa dake bada haske,abinda ya sanya sam idanunsa da hankalinsa basa kan system din kenan. "Alhamdulillah" Ta fada a hankali tana jin wasu abubuwa biyu suna saukar mata. Na farko wani yanayi da kai tsaye zata iya kiransa da qarfin izzar so irin tashi,wata qauna da ta cakuda da kewar abinda zuciya keso din. Ya mata wani fresh,ya mata wani irin kyau me daukan hankali,irin kyan da a kowacce rana ta daga idanunta take sake ganin sabuntarsa a idanunta. Na biyu tayi burin ya kalleta......ko yaya itama ya kalleta kaman yadda ta kalleshi,sai kuma akayi rashin sa'a sam idanunsa basa kanta. "Zamu sake magana anjima hussam,of eeggadhu(ka kula)" Ya qarasa fada yana aza idanunsa akan saamee da tuni ta maida kanta qasa tana wasa da yatsun hannunta kana ya katse kiran gaba daya. System dinma gaba daya ya soma kashewa yana dan aza idanunsa akan agogon dake jikin system din kafin takai ga yin shutting down. Siririn tsaki yaja yana jin kamar kada yau ya sake fita ko ina. Saidai cikin qasa da second guda abinda ya faru jiya ya gilma a idanunsa. Yaren oromo da ya fita da wani irin harshe da accent da yafi kama da irin nasu sak!. Irin karin harshen dake nuna duk wanda yayi yaren idan ba haifefaffen jimma bane yankin oromia,to lallai akwai wani dogon zama da kuma doguwar rayuwa da yayi a qasar. Gilmawar kayan da ya gani dake bashi tabbacin na gidan sarautar agadez ne......sai ya miqa hannu ya dauki daya wayar tasa. Notepad dinsa ya bude,yana sake duba documents din da yayi saving plate number din jiya yana sake duban numbers din da idanu,sai yayi minimizing ya koma contact nashi yana laluben wata number. Bugu daya tak aka daga. Daga daya sashen ya soma gaidashi cikin girmamawa da yaren oromo irin na bakinsa sak. "Aiki nakeso ayimin,amma bana buqatar gaggawa......take your time,inason respond din da zan samu ya zama me ma'ana....." "In sha Allah sir" Ya kirashi da laqabin girmamawa na yaren turanci. Bai katse kiran ba yayi copying numbers din ya tura masa sannan a nutse yace. "Have you seen it?". "Yes sir" Ya fada da qwarin gwiwa. "Fingers crossed" Ya fadi a taqaice. "Thanks" Shima ya amsa masa,sai ya zame wayar daga kunnensa yana miqewa riqe da dukka wayoyin saboda knocking da yaji an masa kadan,yasan kuma zai wahala idan bai kasance maher bane. Ya canka daidai,maher dinne rungume da litattafai a hannunsa. "Minti arba'in yayi saura lokaci ya cika". " Ka jirani" Kawai yace dashi yana takawa a nutse gami da nufar hanyar da zata sadashi da sassan dakunansa yana karbar towel daga hannun salaana,abinda ke alamta masa ya kammala hada masa ruwan wanka kenan. Baisan me yake faruwa dashi ba,ba kuma zaice gashi ba......amma haka kawai yake loosing interest akan aikin. Aikin da shi ya nema gudanar dashi,amma haka kawai yakejin yana barin kansa,wanda baisan dalili ba. Dukkanin yaransa da suke aiwatar da aikin tare sun fishi zama serious. Baisani ba ko saboda sanin da sukayi masa shi din bame wasa da ayyuka bane yasa kowannensu yake cikin hayyacinsa akan aikin ba tare da sunsan shi din ya rasa interest ba. Ya dan jima gaban closet dinsa yana duban kayansa dake tsare a saqale jikin hanger. Mafi akasarinsu jubah ne masu tsananin kyau sulbi da kuma daukan hankalin dake bayyana tsadarsu da darajar zaren da aka samar dasu. Kusan yawancinsu qasar qasar saudiyya ne....qatar oman da morocco. Sai kuma cloak robe da suma bangarensu yake daban,nau'ika da kaloli mabanbanta da suka dace sosai da kowacce jubah da jallabiyya dake cikin closet din. Akwai kurta da kuftas masu kyau,wanda ba kasafau ya fiya sanya kufta ba,yazo ya samesu ne an jeresu cikin closet din,wanda ya tabbatar aikin abdii ne,kuma tafiyayyu ne daga qasar nigeria,bayan wani dare da abdii din ya kashe yana searching qasa da kuma yankin da yafi ko ina iya dinkasu,bincikensa ya sauka a garin kano dake qasaf nigeria din. Sun burgeshi,sun bashi sha'awa sosai,kowacce kusan da hularta 'yar Maiduguri me daukan idanu,amma har yau bai sanya ba,yana ganin kamar bazai zama comfortable ba idan yayi shigar. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 59 ___________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah _____________________________ Sake bin kayan yayi da kallo,a qalla sun kusa set d'ari. A hakan kuma kadan aka tsakura daga suturunsa dake tsakanin addis ababa da kuma jimma,don idan yace yasan adadin suturarshi tabbas yayi qaryar da baisan ta inda zaiyi kaffararta ba. Wani irin ni'imtaccen qamshi cikin closet din kanshi yake bayarwa,ballantana kuma suturun dake ciki,masu abu da abunsu....... Gidan turare ne shi din.....sai ya zamana kuma masoyin turaren,kyautuka guda biyu mafiya girma da tsada da daraja da zaka masa shine. Turare da littafi,sai kuma dabino daya zame masa kusan abincinsa. A kowacce shekara qwararrun masu sarrafa turare daga dukkan kamfaninsa ne suke zama su fidda masa qamshinsa na musamman,irin qamshin da komai kudi dukiya ko mulkinka basa taba fiddashi ko su saidashi,wani unique qamshi ne da babu inda zaka sameshi sai jikin SHEIK HAISAM din. Sun fara haka ne da zummar tukuicin kyautatawa da yakewa dukkan wani ma'aikaci dake qarqashinsa,basusan dame zasu saka masa ba,shi yasa suka maida hakan a mazaunin hanyar rama alkhairansa a kansu. Hakan yana masa dadi,dukkan wani turare da zasu fidda masa yana jin kamar yafi na baya dadi,da wannan ya kasance.......yadda komai na sheik HAISAM yake na daban.......na musamman,haka ma qamshinsa. Wannan qamshin ya nasaka zukatan 'yan mata da yawa......qamshin da muddin kika jishi sau daya ba zaki sake jin makamancinsa ba har abada. Masu kudi da masu mulki da dama daga sassan duniya,sun saka kudade masu nauyi saboda samun irin wannan scent din,amma dukka ma'aikatan,duk da ya basu dama sunqi aminta su bawa kowa wannan TAMBARIN wannan TAG din,wannan alamar ta SHEIK MUHAMMAD HAISAM ce. Wata dark grey colour jubah hannunsa yakai kai. Lafiyayyen dinki aka mata da wani irin yadi me yauqi. Hannu da wuyanta dukka na musamman ne da wani irin button na musamman. Cloak robe ya zaro me hasken kala da zata dace da rigar ya taka yana matsawa a gurin. Tsaf ya kammala shiryawa,yayi tsaye gaban mirror yana daura agogo a tsintsiyar hannunsa. Tun daga nesa idan ka kalleshi zaka ga wani irin kwantaccen kwarjini saman fuskarsa,duk da yau fuskar haisam din adan dinke take,wanda yake da nasaba da yanayin da yakejin zuciyarsa. Haka kawai yakejin ranshi ba dadi,kaman an masa wani abu daya taba ranshi. Ya sani,ba wani wanda ya bata masa rai,hakan wataqila yana da nasaba da shaidan,wanda a kullum burinsa shine ya zunguri zuciyar dan adam,don haka ya daga idanunsa a hankali ya sauke akan fuskarsa data fita sosai da wani irin annuri. Kwantacciyar sumar kansa data habarsa zuwa kuncinsa tayi luf da wani irin baqi me qyalli da daukan hankali,ya lumshe almond eyes dinsa yana furta. "A'uzubillahi minashshaidanir rajeem.....subhanallahi wabi hamdih......subhanallahil azeem". Ya maida qwayar idanunsa akan agogonsa. Tsaiwa yayi cak yana karanta brand din agogon. Yayi kudi da yawa,yayi tsadar da duk wanda yasan kudin agogo yana kalla zai dora zargi a kansa,ya jawo jewelry organizer din dake saman dressing mirror din yana neman me sassauqan kudi,saidai har ya gama lalubensa bai samu daidai da wanda yakeso ba,dole ya dauki qaramin ciki ya daura ya koma neman takalmi. Shima still kaman agogon dai,duk ciki ba wani me qaramin kudi,ya gama lalubensa shima dole hakanan ya dauka ya saka,a ransa yana mita akan abdii. Baisan me ya samu abdii ba,shi ya shirya masa komai na amfaninsa,me yasa yake manta dalilan shigowarsu agadez ne?. Dole komai nasa ya zama moderate,idan ba haka ba da taqi kadan zamansu zai kasa tsaho,duk da yace baisan inda zai sama masa sutura masu qaramin kudi ba sama da wadannan,amma dole ya canza masa wasu abubuwan nashi. Cikin girmamawa drive dinsa ya bude masa BMW din. Yana shirin shiga muryar omari ta tsaidashi. "Captain sheikh" Ya fadi yana takowa a nutse. Baice komai ba sai daya shiga ya zauna,ya daga idonsa yana duban Omari. Gira kawai ya dagewa Omari din,a karon farki kuma Omari ya fahimci yau 'yan miskilancinne a kusa. Maganan da zasuyin me muhimmanci ce,banda hakan zai qyaleshi ne ya tafi,yasan idan 'yan mode din nasa suka sauka zaya nemeshi da kansa. Screen din system dinsa dake hannunsa ya juya ya nuna masa,sai baice masa komai ba bayan ya kalla ya masa nuni da hannu yana matsawa ciki omari din ya samu gurbin shiga. Ba wanda yace da kowa komai,omari na qoqarin qarasa saita bayanan da zaiwa haisam din,yayin da haisam din ya maida hankalinsa ga qari'ar dake fita can qasa cikin motar. Sanda Omari ya yunqura zaiyi magana sai ya dauki remote din dake gefansa ya kashe karatun. "Captain sheikh.......mr Ilaalcha gadi buusuun" Ya fadi yana murmushi ba tare daya kalli haisam din ba. "No more oromo dialogue here mr man......ka kiyaye" Ya fadi yana maida mode dinsa na senior oga kaman yadda yakeyi wani lokacin. Murmushi me kama da dariya sosai Omari ya saki,yayi saluting nasa yana cewa. "Yes sir......but am sorry,Allah saina fadi,mr lowering gaze.......amma komai naka ya zama me daukan hankali.......ta yaya su matan zasu iya kame idanunsa daga kanka?......ka kalli kanka yau kuwa?,kasan Allah?......am very serious,duk yarinyar da tayi falling a kanka saina tayata yaqin samunka?". Ido kawai haisam ya zubawa omari,ganin yadda yake maganar da dukka gaskiyarsa. Sai ya janye idanun ganin Omari shima ya dauke dubansa ya mayar ga system dinsa yana qananun mitoci qasa qasa. "Haka kawai,rashin adalci ne ka dinga tunanin 'yammata ba zasu soka ba,......suma da laifinsu.......mu su somu su gani mana". Bai shirya yin dariya ba sam,duk da dama ba al'adarsa bace,amma duk da haka sai da omari yayi sanadin fitar murmushi a fuskarsa,ya kuma kaiwa Omari dind duka,sai shima ya saki dariya yana wani mazewa. "Allah,da gaske......inajin akwai wani laqanin da kake karantawa a kansu" "Inda akwai Omari saika riga kowa sani......inda kuma akwai da tuni na dade da baka omari,kaje kayi kaji yadda nakeji......banaso omari,sau da dama yawaitar mata a rayuwa mutum irin haka idan baiyi takatsantsan ba,idan kuma baiyi da gaske ba sharri suke zame masa......amma kaima kaji tsoron Allah,ka manta ma'eesha?.....ka manta khansaa?,ka manta batul......" "Qyaleni haka" Omari ya fada da sauri yana boye dariyarsa,sai kawai haisam din ya dauke kai yana qyale Omari din kamar yadda ya buqata. Ba wai shi kadai ba,ba kuma Omari kadai ba,kusan dukkaninsu su bakwai dinnan wani baiwa garesu na musamman. Sun hada wani irin qualities ne da ba kowa Allah yake baiwa shi ba,wannan dalilin ya sanya suka zama masu nuna godiyarsu ga Allah ta hanyar kame kansu da kuma kare mutuncinsu da mutuncin iyayensu dama na addininsu gaba daya. "Duba nan" Omari ya fada yana jiye system din a tsakiyarsu. A hankali haisam ke duban bayanan daya fitar masa din yana saurarensa. "Wadannan guraren,suna daya daga cikin guraren da na samu information gurine na haduwar jama'a masu yawa kuma mabanbanta a qasar nan da garin nan,sannan a nan ne kadai a bincike na za'a iya samun wani da yasan yaren oromo,ko yake yarawa ko kuma ya taba jinsa. Koda taba jinsa yayi zai samar mana haske gurin kusantar samun inda TURAAD ya boye a qasar nan". Shuru haisam yayi yana ci gaba da duban bayanan,kafin a hankali ya janye idanunsa. "Ka hada dukka bayanan ka turamin ta e-mail,sannna ka turawa abba muhammad dawud.......amma ban gamsu da hakan ba". Ido omari yadan zuba masa. Ya iya magana a dunququne da qananun jimloli,mai hankali yana iya faffasata yayi dogon sharhi a cikinta. Duk abinda ya fadi yana da hujja,kuma akwai dalilin da yasa ya fadi haka. "Me yasa kace baka gamsu ba?". " A nan unguwa ko nan garin da muke tabbas akwai yaren oromo" Ya fadi cikin harshen turanci. Idanu Omari ya fidda sanda motar ke gangarawa don tsaiwa a gurin da haisam din yace duka satinnan a nan zasu dinga tsaiwa su jirashi,idan akwai yuwuwar sauya guri cikin satin zai fadi musu. "Ka bari na dawo......ka jira abeer.......ka gaya masa yau su sauya unguwa,su matso maqotan unguwannin da suke kusa da nan,a yau dinnan basai gobe ba......idan na dawo zamu qarasa magana" Ya qarasa fada yana bude murfin motar gami da sanyo qafafunsa waje bayan ya tabbatar ba gilmawar kowa. Da kallo Omari da yayi zaune cikin motar yake binsa dashi. Qaramin murmushi ya subuce masa a hankali. (08187255862 lu'u lu'u) Komai nasa yana nuna sarautar dake zagayawa a jininsa,tsananin nutsuwarsa da kamun kansa,takunsa kadai yasha banban dana maza da yawa,gashi kuma cikin gidan sarautar wasu. Muddin akwai mutane irinsa cikin gidan,muddin akwai mutane masu kaifin hange da dogon nazari irinsa,to babu abinda zai hana su kasa gasgata zukatansu akan cewa shi din malami ne kawai......malamin da zai koyar da yara kawai a biyashi. A nutse yake karantar kowanne sauyawar motsi da yanayi na gidan. Yana wuce kowacce qofa....kowanne shinge yana fahimtar kamanceceniyar yanayin jiya dana yau. "Shalelen sultane.......akhnan yau zata sake baqon da zai zama final choice dinta dana mahaifinta". Maher ya furta qasa qasa wanda yake biye da haisam a nutse. A qofar shiga gidan suka hade da Maher din. Sarai yaji abinda Maher din yake fada amma kuma baiko waiwayo ba bare ya alamta ya jishin. Abinda ya faru jiya sai yaji ya dawo masa fes cikin kanshi. Baya ko shakka yarinyar jiya ce,baya kokwanto ita din ce wani mara sanin ciwo da darajar kan zai sake taka qafarshi muhallinta. Tsaki yakeso yaja,amma yana ganin ba wani dalili na yin hakan,matsalar wasu ce.....matsalar cikin gidan.....matsalar mutanen dake zuwa gurinta. A iya saninshi,babban abu guda daya dake janye hankalin nutsatsen namiji zuwa ga mace shine nutsuwa da kuma tarbiyyarta. Bai ganta a ido ba ballantana yasan nutsuwarta,amma kuma duk inda nutsuwa take tana damfare da tarbiyya.......tarbiyya da bayajin akwai sauran b'urbushinta a gurin. Har qasan ransa yakejin idan ya fadi hakan baiyi laifi ba,don ba tarbiyya a muhallin da d'iya mace zata iya daga hannunta ta mari d'a namiji.....baligi. Ya jima baiga wani abu da bai shafeshi ba wanda yazo yayi masa tsaye a rai irin wannan ba. Besan dalilin da yasa wannan din ya zame masa karan tsaye ba,ya tsaye masa a rai,ya kasa cireshi. "Ya isa" Ya tsawatarwa da zuciyarsa cikin don zare abinda bai shafeshi ba daga ransa. Ya dinga takawa a nutse cikin kebantaccen masallacin da zummar bada faralin sallar la'asar kamar kullum,kafin yakai ga qarasawa cikin makarantar. Ya lura da yadda shiga ainihin cikin masallacin yau ya zama wani kebantaccen abu ga wasu kebantattun mutane,amma hakan bai hanashi takawa a nutse ba yana wucewa ciki abinsa,ba tare da jiran izini ko dama daga bakin kowa ba. Su kansu basusan dalilin da ya sanya suketa dage masa kowanne shinge yana shigewa ba. A cikin jikinsu ba wani me zarrar dakatar dashi ko masa bayanin yau dinma sultane zaiyi sallah ne cikin masallacin tare da surukinsa. Akwai ragowar mintuna da suka rage,wannna ya sanya ya zauna cikin sahu a nutse,ya sanya hannunsa yana fidda wani dan qaramin littafin daya soma dubawa daren jiya bai kammala ba,ya bude ya fara dubawa a nutse,wannna ya sanya kusan duka abinda ke faruwa cikin masallacin bai sani ba. Rufe littafin yayi a hankali sanda yaji alamun fara daidaita sahun sallah,ya miqe a nutse yana gyara cloak robe dinsa. Satar kallonshu Maher yayi,har qasan zuciyarsa burgeshi haisam yake sakeyi. Yayi imanin inda wani ne Allah ya bashi mulki kudi da qarfin iko irin haka,bazai taba aiki da hukumar national intelligence ba,saidai su suyi masa aiki. Inda wani ne....bazai taba yarda a jashi ko a jagoranceshi sallah ba......saidai shi yaja. Yana da tarin ilimin da iya zamansu na kwanakin nan Maher ya fahimta. Baya daukan kansa da nisa,shi yasa da yawa wadanda ke tare dashi basusan irin ilimin da Allah ya hore masa ba. Ranar daya fahimci yarukan da yakeji ya jima yana juya abun. Tabbas rayuwa kowa da irin nashi nasibin. Ya iya French ya iya English,ga amheric ga oromo ga larabci,sai hausa da bata kama bakinsa sosai ba,don bashi da sabga me yawa da ita. Bai bari ya gane yasan ya iya duka yarukan ba,don ya fahimci kamar yana sirranta hakanne. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 60 "Salamu alaikum" Yaji sautin sallama daga gefan damansa. Idanunsa da suka rusuna kadan ya daga yana dubansa na wasu sakanni sanda yake sakar masa murmushi,shima sanye cikin cloak robe da zaunennan rawanin da kana dubanshi kasan qwararru ne suka zauna suka masa wani nadin burgewa saman kansa. "HAKEEM" Sunan yazo kansa lokaci guda,sai yayi qoqarin daidaita fuskarsa yana rage mata daurewar da take dashi tun a dazun,daidai sanda hakeem din ke qoqarin masa bayanin yana tunanin bai ganeshi bane,don ya fahimci kadan daga halayensa na rashin son shiga sabgogin da basu shafeshi ba,saidai shikam ya jima yana burgeshi,tun daga wancan ranar a Riyad har yau ya kasa mancewa da fuskar sheikh din. Musabaha sukayi da juna,haisam ya zame hannunsa,don babu dogon magana kasancewar an fara tayar da iqama. Cikin mintuna bakwai suka kammala sallar. Hakeem na gefansa bai tashi ba yana nashi azkar din na bayan sallah. Ya gane hakeem,a wata musabaqa da suka gabatar a Riyad akan wasu kebantattun litattafan addini daga dukkan qasashen duniya. Kwanaki uku sukayi a wani kebantaccen hotel,wanda kusan duka haisam dinne ya dauki nauyin komai,amma kasancewarsa mutum wanda baison asan yayi wani aiki na alkhairi gudun shigar riya ayyukansa,sai bai bada dama ga kowa yasan shi ya dauki nauyin komai ba. Hakeem yana daya daga cikin wadanda suka tsaya takara......a lokacin haisam ya shiga sahun alqalai na gasar. Tabbas a lokacin yaga matuqar qoqarin hakeem,ya kuma yaba sosai da irin hazaqarsa da yadda ya iya fadin kowacce amsar tambaya daga masu tambayar,duk da daga qarshe ya samu zuwa na biyu ne maimakon na daya,saidai a wajen yin jawabinsa abun ya qayatar da haisam,har ya sanyashi yadan murmusa kadan. Yadda Hakeem din ya bayyana shigarsa qasar kawai nasara ce basai an ayyanashi ba,ya kuma miqa kyautarsa da girmamawarsa dukka ga mahaifinsa,ya kuma ware guda daya yana sake karbar abun magana. "Inaso a bani dama na miqa wannan kyautar guda daya data rage,zuwa ga wani mutum daya da daga yau nakejin ya zamemin wani abun kwaikwayo koda daga nan ba zamu sake haduwa ba SHEIKH MUHAMMAD HAISAM" Iya sunan da haisam din yayi amfani kawai dashi kenan,gudun bayyanuwar identity dinsa. Yana jin dadi idan ya shiga guri yayi mu'amalolinsa da rayuwarsa cikin privacy ba tare da an fahimci waye shi ba. A rayuwa yana jin ba kowanne lokaci bane......ba kuma a kowanne guri bane ya kamata asan wayeshi ba. Wannan kyautar ta Hakeem taxo masa a bazata,saidai abinda yayi masan bazai manta dashi ba. Sosai Hakeem yaso karbar number haisam,saidai hadimansa basu bawa hakeem wannan damar ba,sun rabu yana yawan tuna haisam din,har yau daya ganshi cikin ba zata. Sanda haisam ya kammala addu'o'insa ya shafa a nutse,hakeem ya sake miqa masa hannu cikin sakakkiyar fuskar nan tasa,cikin tataccen larabci ya soma magana da haisam din,don bazai iya tantance wanne yare yakeji ba,kasancewar ko a wancan lokacin da larabci sukayi dukka kwanakinsu da mu'amalolinsu. "Naji dadin sake ganinka sheikh.......ban tsammaci ganinka a agadez qasarmu ba,da nasan kana kusa damu da na jima da nemanka" Murmushi yadan saki masa,baisan me ya hada jininsu haka da hakeem din ba. "Nazo ne ganawa da d'iyar sultane,amma ban sani ba ko zan iya samun damar sake ganinka?" A nutse haisam ya daga kanshi. "Indai baiyi sama da mintuna arba'in ba" "In sha Allah zan qoqarta na kammala a qasa da hakan" *AKHNAN* A zaune take daga gaban dressing mirror din saman stool cikin shigar atamfa embellished holland golden sea blue da ratsin blue black. Wani irin colors ne a jikin atamfda masu wani irin daukan hankali da suka dace da kalar fatarta na cikakkiyar buzuwa. Wannan fatar dake da wani irin glowing da sparkle masu daukan hankali dake nuna zallar kulawa da hutu gami da jin dadi da cikakken sukunin rayuwa da take samu. Wani irin dinki ne na buba akayi mata,kusan zata iya cewa karon farko da zata iya tuna ta sanya atamfa a rayuwarta,don itakam tafi ganewa ready made gown da exclusive abayas,sai designers materials da take bada umarnin zaba mata dinkuna ta hannun LAARA dake kula da closet dinta tana bincika me ya kamata a zuba mata,me kuma ya kamata a cire. Dinkuna dari uku da sittin da biyar duka shekara,domin kuwa sau daya tak take sanya kaya,bata kuma sake maimaita sakasu saidai a sakasu a kayan bayarwa. Shadda kam tana dasu,su dimma bawai sakasu takeyi ba,don kwata kwata iya adadin sanyawarta da shadda zata iya qididdige lokutan. Ko wannan atamfar ma laara ce ta dinkota,ta kuma bawa birra ta gabatar mata da ita,tana ganin zata dace da shigar ta ta yau. Ba wannan bane a kanta a yau,don tana kallon lamarin baqonta na yau shine zai zame mata matsalar qarshe,kuma namiji na qarshe da zata sake bari ya samu daman ganin xagayen fuskarta da furucin bakinta da tsadarsa yafi qarfin kowanne namiji ya jishi. Dinkin ya zauna mata a jiki sosai,ya kuma sake fidda sigar kyanta,qirar jikinta da kuma qara mata wani irin zaunennan kwarjini. Shehnaz na kallonta tana sake gasgata da gaske suturar bahaushe na daya daga cikin suturu da tufafin dake qarawa mutum kyau da kuma kwarjini. Birra ke taje mata doguwar sumarta tana kuma shafeta da tsadaddun mayukan da take kula dasu,saidai duk wannan abun da yake faruwa hankalinta ba'a nan yake ba. Idanu hankali tunaninta dama nutsuwarta gaba daya ta azasu saman ipad din data kafeta saman dressing table din da yake gabanta. Wannan wasan dai......wannan tseren na Hippodrome Niamey shi take bi da kallo cikin kowanne gilmawar second. Har a yau har kuma a kwanan gobe bata da nutsuwa akan faruwar abun. Tunda abun ya faru har zuwa yanxun yana jin sunan MARASA NASARA yana bibiyarta a duk harbawar daqiqa,bata jin kuma zata samu nutsuwar har sai ranar data lalubo WAYE SHI?....Har sai ranar data san meye manufarsa?,me yasa ya zabi ya shirya wasan,ya qirqireshi,ya kuma gabatar dashi?. Meye dalilin bata mata LAMBARTA da ita kadai keda mallakinta tsahon shekaru?,me ya yiwa thunder data kasa controlling dinsa?,har dai shine yayi controlling dokin da kaf cikin dawakanta tafi ji dashi?,dokin da suke communicating ita dashi da tsananin sabo tamkar dan adam?. A hankali aisa ta tura qofar tana shigowa da sallama,saidai shehnaz kadai dake kwance rub da ciki saman gado ce ta amsa,don akhnan din ko motsawa batayi ba bare tayi yunqurin amsawar. Abinda ya ja hankalin aisa din,ta taka a nutse zuwa inda take,sai tayi tsaye a bayanta tana duban abinda take kalla,wanda clip din yazo daidai inda take fadowa ya kuma tallafeta da hannunsa guda daya. Ita da aisa din lokaci guda hannuwansu yakai kan ipad din,kaman aisan tasan niyyar akhnan nayin wurgi da ipad din ta samu nasarar rigata dauketa tana kasheta ta wurgawa shehnaz ita. Idanunta ta aza kan akhnan,duk wani mode nata yana nuna fushi da bacin rai,wanda aisa din takejin sam baima dace ta doshi baqonta a haka ba. Muddin haka zata kasance komai zai iya faruwa.....kunyar da dukka aka tattaru ana fatan kada yau a jita zai wahala ba'a shata ba. "Meye amfanin kallon abinda ya riga ya faru......banda yiwa kai tanadin bacin rai?" Aisa ta furta tana duban akhnan da fuskarta tayi wani irin kyau tsakanin surfanin dake wuyan atamfar bayan gama daure mata gashin da birra tayi. Hannu ta sanya tana ture dankwalin da birra ta aza mata a kai da nufin daura mata,ta dubi aisa din tana juyo da kujerar gaba daya tana fuskantarta. "Kina zaton wannan tarihin zai tafi ne a banza?......kina tsammanin xan qyaleshi ne?,yayimin abinda,ya kuma bace ba tare da yabar wani alama ko guda da zata bayyana wayeshi din ba......kina zaton duka hakan ya faru ne bada wani shiri ko manufa ba?......na rantse saina laluboshi a duk inda ya shiga......na kuma rantse sai na sanyashi ya kwashi kashinsa a hannu......diyar SULTANE MUHAMMAD HAMMUD NAKE FA". Idanu aisa ta janye a hankali tana sauke ajiyar zuciya. A yau ne ta sake yadda da akhnan din baudadden halinta na halitta ne......kafiyarta kuma a jininta take,bata tunanin akwai wani yanayi ko wani dan adam da zai iya canzata "Est-ce que c'est la seule chose qui vous dérange?(wannan ce kadai damuwarki?" Ta tambayeta tana riqe da qugunta tana dubanta. Sai data daga fararen idanunta masu surkin blue ta watsawa aisa,sannan a nutse itama tace "Est-ce qu'il y a autre chose?(akwai wani abunne daban?)" Idanu aisa ta bita dashi,ta fuskanci da gaske idan ta biye mata zasuyi rigima ne,sai taja tsaki kawai tana matsawa inda shehnaz ke kwance. Harara ta watsawa shehnaz din tana dubanta. "Ba wani sauran abinda zakiyi ne?" Ta furta cikin gatse,don ta fuskanci wani lokaci plan din akhnan yana zuwa daidai dana shehnaz. "Ques veux-tu que je fasse?(me kikeso nayi?)" Ta fada cikin rashin ko in kula. Ta sani,ita ko aisa basu isa canza ra'ayin akhnan ba. Mayafinta ta zara wanda birra ta ajiyeshi daga gefe da nufin idan ta kammala shiryata ta bata tayi amfani dashi. Lullubawa tayi kawai saman kanta ba tare data damu da d'aura dankwali ba ta soma takawa tana fita a dakin,sai su dukka suka bita da kallo cike da mamaki. *FALAAK* Wata baquwar dabi'a ce a tare da ita,damuwa da duba kowanne lungu da saqo na fuskarta tanason tantancewa ko akwai wani abu daban da bai kamata ta fita dashi ba?. Ko akwai wani abu da baiyi a fuska ko kuma jikinta ba?. Ita kanta batasan hakan yana faruwa da ita ba,har sai da taji dariyar badee'a. Cak ta tsaya daga goga lipstick din da takeyi tana duban badi'a din. "Lafiya?" Ta fadi a mamakance. Kai badee'a ta girgiza tana dubanta. "Bansanki da irin wadannan sanaben ba uwar dakina......yau din da kikeyi sai abun yake bani dariya da mamaki". A hankali ta maida dubanta ga lipstick din hannunta,wanda ba wani color gareshi ba,sai ta maidashi saman madubin a hankali tana ajiyeshi. "Dama kin qarasa,yayi miki kyau sosai" Badee'a ta fada tana duban ta. Kai falaak ta girgiza tana daukar wayarta dake gefe. "Muje badee'a" Ta fadi tana jin wani fargaba da bugun zuciya yana qaruwar mata. Tun daga safiyar yau take lissafin adadin awannin da ya rage su shiga karatu,a duk sanda daqiqa daya ta ragu kuma sai ta samu kanta cikin wani matsanancin harbawar gudun zuciya. Sai takejin kamar me tsoron haduwa dashi,tsoron kuma daya cakuda da zumudin zuwan awannin haduwar. Ta sani,zallar kwarjininsa ne yake dukan idanu da zuciyarta,wanda batasan dalilin hakan ba,kwarjinin da har a jiya data kwanta tana wassafashi ne cikin idanunta. Tayi karatun addini daidai gwargwado hannun malamai kala kala a france sanda take hannun hairaan. Kusan kuma dukkaninsu babu dan africa,amma yanayin da takeji a yanxu bata taba jin makamancinsa ba. Bata samu morsa ba,an shaida mata tana ganawa da baqi,wannan ya sanya kai tsaye suka wuce ita da badee'a wadda ke dauke da wasu daga cikin litattafan da yace zasu sauya,duk da ba duka aka samo ba. Wasu babu su a kasuwa,har sawa morsa tayi aje a duba amma an tabbatar mata babu su,sai nan gaba za'a shigo dasu daga misra. A nutse yake takowa cikin gurin bayan Maher ya juya tun daga shingen qarshe. Wanda hakan umarni ne daga haisam din,bawai don ba za'a bar maher din ya shigo ba. Wannan qasaitaccen qamshin da a jiya ya sanyata laluben kalar turaruka da dama ko zata samu wanda qamshinsa yayi daidai dashi shi ya fara marabtarta,shine kuma ya shaida mata wanzuwarsa a gurin,sai ta daga kai tana jin wata irin fargaba qwayar idanunta qasa qasa tana dubansa,kafin ta zame idanun nata can qasa daga barin kallonsa gudun kada ya ganta,sai takalman da suke qafarsa kawai take iya kalla. Idanu ta zubawa takalmin tana son tuna wani abu. Tsahon wasu sakanni sannan ta tuna. Irin takalmin sak da morsa ta taba siyawa me martaba cikin kayan gift da takan hada masa a duk shekara na barka da sallah. Kudi ne masu nauyi da har falaak ta dinga cewa. "Sultane dan gatan morsa,Allah sarki ni auta falaak,morsa nan na kawo na dubu dari biyar kikace yayi tsada da yawa,ni din macace da zanje gidan wani,ba lallai komai na samu a gidanmu ba na sameshi a gidan mijina......amma ga sultane da takalmin......" Daquwa morsa ta watsa mata tana jifanta da harara,saita saki dariya,ta dauki takalmin kawai tana juyashi,don sosai ya tafi da ita. Idanunta ta janye a hankali tana laluben fuskarsa,kallon fuskar daya sake tsananta bugun zuciyarta. Wani washewa fuskar tasa tayi sosai cikin lullubin da yakanyi ya suturta habatsa har zuwa karan hancinsa,wanda hakan ba kasafai yake bada daman ganin fuskarsa gaba daya ba. Fuskarsa ta yalwata da sakewar da ba zaka kirata murmushi ba,yana riqe hannun Aeeda sarkin saurin sabo da mutane,wadda kuma ko sau daya mutum yayi mata me rabata dashi dai Allah. Aeeda irin yaran nan ne masu shiga rai,ba ruwanta da baka yinta ko kana yinta,itadai indai kayi mata shikenan,sauran matsalar taka ce. Tana ankare dashi,da salon takunsa dinnan dake nuna lallai akwai digo na jinin sarauta a jikinsa ya qaraso section din su Aeeda,ya zare takalman socks yayi saura a qafarsa,yahau saman tattausar kujerar da tafi zubi da ni'imtacciyar shimfida me tudu,ba kuma tare daya daga ido ko sau daya ya kalli sashen da suke zaune ita da badee'a ba Yanayin zamansa kawai sultane mahaifinta ya haska mata,ire iren xamansa kenan a fada ko a cikin gida. Wani zama ne na musamman dake sake fidda kwarjini sosai ga sarakuna,sai ta zuqi wani irin numfashi,kafin kuma ta ajiye badee'a ta rigata magana. "Hodijam.......yanzun wannan malami ne me koyarwa?" Ta jefawa falaak tambayar tana me mantawa da girman tazarar dake tsakaninsu. Tun dawowarta jininsu yazo daya da badee'a,kuma morsa ta sanyata cikin hadimanta na kusa,don ta yarda da hankali tarbiyya da kamun kan badee'a din. Bugu da qari falaak tana buqatar wani a kusa da yayi rayuwa sosai cikin agadez......cikin masarautar agadez da zai dinga kwatanta mata yadda abubuwan gidan suke,don ta jima rabonta da qasar,tun batafi shekaru bakwai kacal a duniya ba. "Me kika gani?" Falaak ta tamabayi badee'a tana dubanta a hankali. "Allah ya huci ranki idan har nayi maganan da ya sabawa tarbiyya da kamata. Kwarjininsa da kyansa ba na irin gama garin mutane bane,zamansa uwar dakina kadai yana alamta ba mutum bane irin kowa......baiyi kama sam da jinsinmu ba.......duk da yana zubi da kamanni da buzaye.......amma akwai banbancin launi a tattare dashi" Tayi maganar qasa qasa,saboda yadda jikinta yake bata kaman zaiyi kaifin jin magana. "Amma da French yake magana......saidai bayan wannan bansan ko yana magana da wani yaren ba na daban". Falaak ta fada tana neman qarin haske daga gurin badee'a. Kamar ruwa ya cisu haka sauran kalaman dake bakin kowannensu ya dauke tsaf saboda daga idonsa da yayi ya kallesu sau daya,cikin qasa da second biyu kuma ya sauke kansa qasa yana duba ayyukan Aafreen. Dukka suka rufe babin maganar,don daga ita har badee'a ba wanda ya qara cikakken motsi ma,har mintuna ashirin nasu Aafreen ya cika,Aafreen din kuma ta tako tayi kiransu rungume da books dinta. 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 61 Daga ita har badee'a cikin nutsuwarsu suka qara wajen,suka zare takalmansu suna zama saman shimfidar da aka raba littattafai gurin zaman mutum biyu. Koda baiyi magana ba falaak ta gama fuskanta,litattafan da zasu fara karantawa ne ya basu ba tare da tambaya ko bin ba'asin sun siya ba?. Wani irin burgeta taji yayi,ta buda baki ta soma gaidashi da harshen faransanci,ya amsa a taqaice,gaisuwar badee'a ma ta biyo baya. "Ga litattafan da zamu fara nan.....amma bana karatun banza,kowanne rana kafin mu dora sabon karatu zaku maimaitamin abinda muka karanta jiya don nasan abinda nakeyi din ba wahala bane" Ya fada cikin nutsuwarsa da kamewarsa data qara masa wani irin kwarjini. Da gaske ko zakayi wasa da komai amma kada ka yarda kayi masa wasa da karatu,baya daukan wannan kusan tsakaninsu hussam rumaisa noory dama dukkan 'yan uwansa sunsan da wannan. "In sha Allah" Falaak ta fadi tana daukar littafin da yace dashi zasu fara. Iska ta shaqa sosai tana zuqar daddadan qamshinsa har cikin hunhunta. Iya riqe littafin kawai da tayi ba tare data matso dashi kusa da hancinta ba tana iya jin fitar wannan qamshin nasa na musamman daga jikin litattafan. Ta tattara dukka nutsuwarta tana sauraren muryarsa dake fita da wani irin nutsuwar da dole kaso karatunsa......dole kuma ka fahimta ko don irin taushin da amon sautinsa yake bayarwa. *AKHNAN* A qasaicenta take takowa zuwa gurin daya zame mata na al'ada gurin ganawa da baqin da suka zamewa rayuwarta alaqaqai,cikin fata da sanya ran a yau wannan din ya zama shine baqo na qarshe da zata gani a gabanta. Duk kuwa da irin yadda zuciyarta ke sake nanata mata cewa,hukuncin sultane fa wani abu ne da babu wanda ya isa ya tayar dashi,duk da zuciyarta na d'arsa mata,lokaci bayan lokaci cewa.......tana taku ne zuwa ga muhallin da zata gana da mijin da sultane ya zaba mata......final choice kuma da take dashi,amma zuciyarta na gaya mata cewa wani abu ne da ba tabbatacce ba.....wani abu ne da bazai tabbata ba,sultane bazai taba aikata hakan ba,ya fadi ne kawai don ya tsoratar da zuciyarta zuwa ga karkata ga aikata abinda yakeso. Haka kawai ya samu kansa cikin fargabar da baisan dalili ba.......lokacin da ya dauka yana jiranta sai yaji ya masa tsaho. Sau daya tak ya taba samun damar ganinta,amma kuma zuciyarsa ta jarabtu da sonta sau babu adadin da baisan yawan da zai qayyade masa ba. Sake juya qaramin littafin hannunsa yayi,yana karantawa ne kawai don ragewa kansa lokaci,amma ba don yana fahimtar me yake karantawar ba,sai ya sake budewa yana ci gaba da dubawa ko hakan zai taimaka masa ya sake rage yawan lokutan data barshi a zaune. Akwai wani yanayi a wajen wanda zata iya cewa baqo ne a idanunta. Batasan wanne irin baqo bane yazo gurinta,amma babu wannan securities din masu yawa......baqin fuskokin da suke alamta cewa dukkaninsu hadimai ne kuma ma'aikata ga baqonta. Mamaki ya sake cikata.....wanne irin baqo ne yazo gurinta?,wanda babu wani kwarjini a tare dashi?,babu wannan haibar da cikar yawan adadin 'yan rakiyar da suke nuna matsayin da yake dashi. "Waye shi birra?" Ta tambayi birra dake biye da ita kai tsaye ba tare data waiwaya ta dubeta ba,saidai ta xubawa qofar data rage da zata sadata da ainihin gurin da kuma inda yake. K'asa birra tayi da kanta,har cikin ranta tana jin fargabar sanar mata wayeshi?. Ba iya yau ko jiya ba take tare da uwar dakinnata ba,tasan dukkan wasu zabuka nata,tasan dukkan wani buri nata......ta kuma san wanne irin nau'in miji take lissafi?. "Ke nake saurara" Akhnan din ta fadi tana sake ragi karsashi tafiyarta,duk da dama tana takawa ne da salon tafiyar nan tata me kama da tafiyar dawisu. "Tilon d'a guda daya ga limamin babban masallacin juma'a na zinder........." Birra ta fada cikin sanyin jiki. A sukwane ta waiwayo ta zubewa birra din wani irin kallo. Dan limamin babban masallacin juma'a?......limami kuma?......ita khadeeja sultane muhammad?,ita biftu?.....ita din mamallkiyar hamshaqin kamfanin da kaf fadin africa babu yashi?......ita din diya tilo ga sultane muhammad?. Abubuwa da yawa ne suke mata kai kawo,bayan tarin tulin tambayoyin da take dasu,saidai kuma GIRMA wani abune dake yawo a jininta......hadimanta kuma har kullum hadimanta ne,kusanci ko mu'amalar yau da gobe ba zata sauya wannan ba,don haka birra ba abokiyar wannan maganar bace.......ba kuma huruminta bane. "Ki jirani a nan" Ta furta tana juyawa a nutse da qasaitaccen takunta tana sanya kai. Tun daga nesa ta zuba masa idanu,cikin wannan salon nata da ba kasafai kake iya karantar kai take kalla kai tsaye ba. Fuskarsa ta mata kama da fuskar data taba gani,amma ta manta a ina?,wayeshi?,kasancewarta wadda bame shiga hada hadar jama'a ba. Uwa uba dukka wani abu daya hada da maza a ciki bata sanya kanta cikin sha'aninsu,saboda jin martabarta da izzarta. A hankali ya rage kaifin kallon da yake mata yana kiran sunan Allah har labbansa suna motsawa. Da gaske.......kaman yadda ta tsaye masa a rai tun a gani guda daya tak daya taba yi mata a zahiri muraran haka take. Yadda zuciyarsa ta shagaltu da tunani da kuma imagination nata har abun yafi gaban haka a zahiri......da gaske d'aya ce tak cikin mata.....duk kuwa da cewa ba ma'abocin kallon mata bane shi. HAKEEM sunan yazo kanta dab da zata isa inda yake. D'a ga limamin babban masallacin juma'a na zinder. Tabbas wannan shine wannan hakeem din,wannan hakeem din da sultane suka taba ganawa da mahaifinsa a satin da zata bar agadez ta koma Niamey don kula da kamfanin da sultane din ya mallaka mata sukutum. Idan bata manta ba,wannan hakeem dindai shine wanda mahaifinsa ke qorafin yaqi karatun boko.......wannan hakeem din shine dai wanda mahaifinsa ke qorafin ya zabi karantarwa,yaqi amsar dukka wata harkar business ko fita qasashen waje da mahaifinsa keyi sai qaninsa ya dora akai.....wannan hakeem din dai shine taji mahaifinsa na dariya yana fadin ya gaza zabar matar aure,kamar tsoron mata yakeji,ba kasafai yake tsaiwa da mace suyi doguwar magana ba......wannan hakeem din da shine yaqi kasuwanci duka ya miqa ragamar kula da komai nasa ga qaninsa.......wannan hakeem din da bai iya doguwar magana da French sai larabci kawai da asalin yarensu na zinder yaren mahaifi da mahaifiyarsa.......wannan lusarin HAKEEM din......wannan LUSARIN MIJIN shine sultane ya zaba mata?. Tana zaune a wani gefe daban na dakin hutawar sultane tana jira ya sallami baqonsa yayi mata signing din da zai mata taji dukka wadannan maganganun. Ta tabe baki tana maida hankalinta ga takardun gabanta,cike da mamakin failure irin ta wannan mutum da suke magana a kanshi cike da mamaki. Ya shigo ya samesu a dakin hutawar.......maganganun da sukayi a kansa ya sanya ya daga idanu sau daya tak ta kalleshi don taga wanne irin mara sanin ciwon kaine wannan?,a sannan ta soma ganin fuskarsa. Tun a sannan taji baiyi mata ba,bawai don akwai wani abu daya faru ba.....a'ah,sai iya tattaunawar da taji su sultane sunayi a kansa,tun a sannan kuma ta laqaba masa sunan KASASHE a ranta. Ya bace mata sam akai,don tun daga wancan ranar bata sake ma wani tuna abinda ya danganceshi ba,sai a yanxun da ta kalli fuskarsa komai ya dawo mata. Sake jagulewa ranta yayi,ta sanya hannunta a goshi ta dafe kadan,sannan ta dauke yana yarfar da hannuwa,tana jin yadda gaba daya bacin rai ya cika nata qirjints,har tana jin babu wani space daya rage. Bacin ranta ya sake ninkuwa sanda take dubansa duba irin nakai tsayen nan ganin yadda ya gaza sanya idanunsa cikin nata. Abune me wahala ta kalli namiji irin haka,amma baqo dai irin HAKEEM rashin darajarsa ta zarta ta kowa a gurinta. Tabbas tun daga sanda ta samu labarin morsa safiyya ta taka wata rawa a zuwan baqonta na yau tayi imanin babu wani alkhairi ko abun arziqi a ciki. Ba wani alkhairi kwata kwata da zaizo daga matar zuwa gareta,sharri ce ita!.......duk kuma wani abu daya danganceta din sharri ne. Qoqarin gyara mata kujerar da zata zauna yayi,amma zafin naman da takeji yau a jikinta ya sanya ta rigashi aikata hakan "Nasan za'a rina......daga yanayin gidan gaba daya jikina ya bani wani qasqantaccen ne yazo gareni........ashe arahata har takai haka?" Ta qarasa maganar idanunta na nuna zallar kaifin fushin dake cikin su,ta kuma dauki qafarta daya ta dorata saman daya cikin wani yanayin zama dake nuna zallar izzarta da kuma izgili ga hakeem dake zaune kawai yana dubanta ba tare daya motsa ba. Idanunsa ya dan runtse,yaji zafin kalamanta,amma kuma tunawa da yayi itadin macace me raunin hankali sai yayi qoqarin basarwa. "Sallama ya kamata ki fara yi koda ba zamu gaisa ba ko gimbiya?". Manyan fararen idanunta masu blue din qwayar idanu ta watsa masa,abinda ya sanya kwarjinin nan dake tattare da ita ya ratsashi. "Gaisuwa......ko sallama,dukkaninsu ana yinsu ne ga mutumin madaukaki me daraja........wanne gangancinne yakai ka gabatar da qudurinka a kaina?......har ka nemi ganawa dani?" Ta masa tambayar tana tsareshi da idanu kaman yadda uwa kewa d'anta. Murmushin qarfin hali ya saki a hankali. Ya sani,tunda har bada son ranta bane,zai iya fuskantar kowanne qalubale da kuma turjiya kafin ya samo kanta. "Qauna ce.....da kuma son kasancewa mijinki in sha Allah". Idanunta ta janye,wani dariya data maida gurbinsa da murmushi ya subuce mata,abinda ya sake fidda zallar ainihin kyanta,kyan daya daki zuciyar hakeem kai tsaye. Sakanni kusan biyar sannan ta gyara zamanta tana zube masa idanunta. "Kai yanzun a naka ganin akhnan ta dace da maqasqancin mutum irinka?" Ta furta da wani irin kaifi a muryarta da idanunta,kamar ta bashi damar bata amsa ne,kafin kuma ta sake cewa ".....Na yarda......cikin nau'in mutanen da sukafi kowa son zuciya......tsaurin ido da kai kai inda Allah bai kaisu ba irinka ne.......mutanen dake iqirarin ilimin sanin Allah da annabi.........maha'inta masu ci da addini........inaso ka sani.......cikin nau'in mutanen da na tsana.......bazan kuma taba iya aurensu ba koda NI DASU KADAI MUKA RAGE A DUNIYA sune gidadawan masu ci da addini da sanya rawani a kansu da daukan litattafai da sunan su din malamai ne......" Ba ita daya ba,hatta da badee'a ta fahimci karatun yana shigarta sosai,don itama ta sake nutsuwa,ta kuma tattara dukkan hankalinta guri guda. Saidai a sanda muryar akhnan da hakeem ta fara ratsowa inda suke sai dukka hankalinta ya soma rarrabuwa gida biyu,da wani irin nauyi da kunyar yau kuma me zata ce da hakeem?.......yauma yana jin abinda take furtawa ko kaman jiya ne?. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 62 A nutse ya sanya hannunsa ya maida bangon littafin ya rufeshi,bawai don sun gama karatun ba ko kuma yakai inda ya kamata ya tsaya ba. Tun daga sanda ta fara magana da hakeem yake gayawa zuciyarsa ba huruminsa bane........ba abinda ya shafeshi bane,wani sha'ani ne da bai shafeshi ba.......bai kuma hada dashi ba sam.......saidai kuma wani irin suka kalamanta suka fara yi suna sauka saman qahon zuciyarsa daya bayan daya da wani irin kaifi,duk kuwa da cewa bada shi take ba,batasan ma da wanzuwarsa a gurin ba. Shuru gurin ya dauka,kaman yadda baiyi motsi ba haka ba wanda ya motsa tsakanin ita da badee'a. Ko ina jikin falaak rawa yake,takaici da tashin hankali yana cikata. Koda baiyi kowanne motsi ba ta tabbatar a yadda gurin yayi shuru,dukkanin maganganun da Akhnan taci gaba da jifan Hakeem dasu suna sauka yadda ya kamata cikin kunnuwasa. Shurunsa na nufin abubuwa da dama,ya dunqule hannunsa guri guda yana jin zafin kalamanta tamkar shi take gayawa. Me hakeem yakeyi?,me hakeem yaci gaba da tsaiwa yana yi har ta samu daman ci gaba da zuba masa wulaqantattun kalamai haka?. Mutum nutsatse irin hakeem din,wanda yake da quality din daya tabbatar yafi nata duk da taqamar sarautar da takeyi?!. Har abada babu wata daraja ko matsayi da zaiyi daidai dana mutumin da yake dauke da ilimin addini a kwanyarsa!......me hakeem yakeyi?!. Ya sake tambayar kansa yana jin yadda jijiyar kansa ta fara tashi,kowanne kafa na jikinsa ya soma fidda gumin da hakan yake bashi tabbacin lallai ransa ya soma baci. Baya jin zai iya ci gaba da zama a gurin kunnuwasa suna jin furucinta da daidai yake da zagin kowanne mutum me kamanceceniya da hakeem din "Subhanakallahumma wabi hamdik,ashahadu an la'ilaha illa ant,astagfiruka wa'a tubu ilaik" Kawai ya rufe da ita yana qoqarin saisaita muryarsa da yakejin yanayin fitar sautinta ya sauya,ya miqe a nutse yana sanya takalminsa,wanda yayi daidai da isowar daya daga cikin hadiman me martaba. "Sheikh......me martaba yace a shaida maka......yana buqatar ganinka idan an bashi dama". Idanu yadan xuba masa yana mamakin fitar kalar furucin daga bakinsa. Ya sani,ba yaren kowanne basarake bane hakan......ya nema izini daga wajen wanda yake ganin yana rayuwa ne a qasansa,umarni na kai tsaye shi sukafi ganewa,amma shi din izini yake nema ayi masa. Wanne irin uba ne wannan da baiyi sa'ar diya ba?,wanne irin uba ne wannan wanda sam bai fidda iri me kyau ba?. Kai kawai ya gyada masa,yana jin daukewar sautukanta masu zafi,wanda yake tunanin numfasawa ta tsaya yi,ko kuma ta kammala fadin dukka abinda yazo bakin nata ne. "Idan burinka ko mafarkinka shine aure na......ina me shaida maka.....ni Akhnan nafi qarfinka har abada......zaka mutu kuma da wannan burin naka ne" Ta qarashe maganar sanda ta miqe tsaye,sannan ta juya da dan hanzari tana takawa don barin gurin. A yadda takejin zuciyarta a sannan kuka kawai take da buqatar yi,banda kukan ba wani abu daya kamaceta........saboda zafin da takeji a ranta ya zarta ta iya cinyeshi kota hadiyeshi. Saidai kuma babbar faduwa ce a tare da ita wani daban yaga hawayenta......wanin da ba sultane ko mammina ba......koda morsa sai ya zamana dole ne take bari ta hangi fitar hawaye a fuskarta. Tana ji a ranta a wannan karon itama a shirye take ta bijirewa umarnin sultane,a shirye take tayi fito na fito da umarninsa....... Gwaraba tariyo mata dukkan mazan da suka taba takowa domin nemanta......sultane ya zaba mata koma waye a cikinsu akan hakeem . Hakeem fa?,hakeem din da rana ta farko data fara saninsa a rayuwa tayi masa laqabi da lusarin namiji.......hakeem din da bata tunanin ko digo qwara daya yahau cikin kaso dari na kalar zabin da take dashi idan har ya zama dole ma sai ta rayu da d'a namiji......hakeem din daya kasance malami,wanda baida kowanne irin experience na rayuwa........baida kowacce irin gogewa a rayuwa,baisan ma me duniya take ciki ba. Banda littafi rawani da zaman karantarwa ba wani abu daya sani. Kai tsaye taji ba inda ya dace ta nufa sai gurin mammina.......ita daya ce ita kadaice kuma fatanta,ta tabbatar zata cika mata alqawarin data dauka na tsaiwa a gefanta da kuma tsaiwa a bayanta a duk sadda irin hakan ta faru. *MAMMINA* Ci gaba tayi da irgen mintuna daqiqu da kuma sakanni,tana jin ba wata kujera cikin parlor din da zata iya dauke nauyin abinda ke saman ruhi da zuciyarta ballantana ta zauna a kai. Wannan jiran ya zame mata wani irin jira na daban,irin jiran da yake da tsaho da kuma tsauri duk da fata da take dashi cikakke da kuma tarin yaqini. Ta riga ta d'ana ta kuma dasa gami da harba komai......wanda abune me wahalan gaske wadannan shingunan.....wadannan turakun dukkaninsu ace an shuresu. Bakin window ta qarasa,ta saka hannu ta bude labule kamar wadda iskar dakin ta sassanyar A.c ta yiwa kadan,batakai ga ajiye hannunta ba lafuzzan da take faman jira suka sauka mata a kunnenta. "Yalwa ce" "Qaraso" Ta bata umarni kai tsaye ba tare da taji qarshen maganar tata ba. Da hanzari ta baro bakin window din,ta kuma tako da dan hanzarin tana zama hannun kujera,yayin da yalwa ta zube a qasa fuskarta da murmushi. Iya murmushin fuskar yalwa ya isa ya gaya mata kalar nasararta.......iya wannan murmushin kadai ya gama bata dukkanin amsar da takeso,amma saidai tana buqatar taji ta kuma sake samun tabbaci daga bakin yalwa din. "Allah ya tayawa ayyukanki......komai ya tafi daidai......kamar dai kullum,kamar kuma ko yaushe,shima dai ta tankwabar da tayinsa,ta kuma watsawa sultane qasa a ido,don tozarcinsa yafi kowanne kalar tozarci da ta taba yiwa wani". Wata ajiyar zuciya me nauyin gaske ta sauke wanda take cakude da murmushi. Ta qanqance idanunta sosai tana sakin murmushi gami da hango yadda nesanta ta dawo kurkusa.......tana kuma hasashen yadda komai yake tafiya daidai,hanyoyi kuma suke gyara kansu da kansu. "Da kyau!........" Sai ta miqe tsam tayi taku biyu. "Duk yadda zataso ganina yanzun kada ku bari hakan ta faru,banason na zama ta farko da zata gayawa qudirinta,kaman yadda banaso ta fara haduwa dani kafin taga sultane.......ki yiwa Souleman magana,a fiddo min mota,zanje ziyarar awa daya,kafin na dawo na tabbatar komai ya kankama". Qasa yalwa tayi da kanta tana jinjinawa basirarta,sannna ta furta kalmar. "An gama" Ta amsa mata tana miqewa da duka hanzarinta. *FALAAK* Haka kawai ta dinga jin hawaye suna taruwar mata a idanu,hawayen takaici hawayen kunya......hawayen mamakin yadda yaa akhnan din ke iya rufe idanu taci mutuncin masu mutunci. Tayi tsananin mamaki a abinda ya faru jiya,ta dauka iyakar abun kenan,saiga wata sabuwa kuma akan hakeem. Koda baqonta na jiya ba wani daraja ko martabar komai a tattare dashi......amma hakeem yakai a martabashi da darajan ilimi da alqur'anin da yake dauke dashi. Bata taba zato ko tsammanin abun nata yakai har haka ba.......sai a yanxun,tsoro yana sake shigarta,tsoron kada Allah ya jarabceta ko ya jarabcesu da wani mummunan abu sanadin wulaqanta ma'abota alqur'ani. Ba zata manta yadda take ganin sultane yana girmama duk wani mahaddacin qur'ani ba,tun tana mitsitsiyarta......tun tana qaramar kuma tana iya tuna sanda yake musu alqawura da dama ga duk wanda ya samu haddace qur'ani a cikinsu. Duk da bata haddace duka ba,ta haddace kusan izifi ashirin a ciki......mutuwa ce kadai zata sanyata ta manta irin shagalin da sultane ya hada cikin masarauta saboda samun izifi ashirin din da tayi,ya tabbatar mata na izu sittin dinta sai yafi haka,saidai bata samu wannan damar ba,auren hairaan ya tashi ta kuma dauketa zuwa France. 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 63 Wani irin tashin hankali takeji idan ta tuna yadda taga fuskarsa. Ba wani abu daya nuna saman fuskarsa......saidai ga duk wanda yayi masa zuzzurfan kallo zaisan cewa akwai wani abu me nauyi daya sauka ya kuma nutsa can qasan zuciyarsa. "Kiyi haquri......ranki ya dade hankula sun fara yowa kanki" Badee'a ta fadi qasa qasa tana biye da falaak. Ba wannan bane kawai burinta,burinta shine ta isa ga momma.......burinta ta ganta gaban momma. Wani irin hali dabi'u da kuma dabi'a ce wannan tattare da yaa biftu din?.......wanne irin izza ne haka tattare da ita da takejin tana daidai da wulaqanta kowanne kalar d'a namiji?.......mutane masu mutunci......masu yakana masu kima da martaba?,amma take iya tsaiwa gabansu ta yage dukka wannan?. Sam morsa safiyya bataji shigowarta ba,sai rungumeta ta baya da taji tayi,bugawar da zuciyarta takeyi tana ratsa gadon bayan momma din kwatankwacin mutumin da yaga wani abu me matuqar ban tsoro. "Hasnunallahu wa ni'imal wakeel" Morsa safiyya ta fada tana sakin mayafin hannunta ta kuma juyo a hankali tana zare falaak daga jikinta tana dubanta. Ko falaak bata ce mata ba lafiya ba ita din tasan ba wani batun lafiya sam a tattare da falaak din. "Me ya faru?" Momma ta tambayeta bayan fa zaunar da ita ta kuma zauna kujerar dake fuskantarta. "Ya biftu......" Ta kira sunan muryarta na karyewa,abinda ya sanya matsananciyar faduwar gaba kenan ga morsa safiyya. "La haula wala quwwata illa billah" Ta fada can qasa tana fatan kada kunnuwanta suji cewa Akhnan din tayi abinda ta saba. "Abinda ya saba faruwa ne ya faru?" Ta tambayi falaak a hankali kamar me tsoron furta tambayar. Kai falaak ta daga mata,hawaye na taruwa a idanunta. "Momma.......a kunnensa jiya yaji ta mari wani......yau ma a kunnensa yaji yadda take cin mutuncin......" Sai ta kasa qarasawa saboda kukan daya qwace mata. "Waye?" Morsa ta tambaya tana duban falaak cikin son jin abinda ya taba zuciyarta har haka. "Sheikh mana momma......sheik muhammad" Numfashi me nauyi ta zuqa daga qofofin hancinta zuwa hunhunta,don tashin hankalin da take ji a dukka zuciyarta dama jikinta ya sanya bata tuna dashi ba. Ta fidda idanunta waje kadan. "Farawar da gamawar dukka yana gurin dama?" "Yana nan momma.....mun fara karatu......karatun yau ko gama shi bamuyi ba......bai nuna ba ko a fuska yaji komai ba tsakanin jiya da yau......amma nayi imanin yaji". Ta qarasa fada tana fashewa da kukan da yafi na dazu. Shuru momma tayi tana zubawa falaak idanu. Yanayin kukan nata da yadda take yinsa da dukka zuciyarta sai ya rarraba mata hankali. Ba komai falaak kewa kuka har irin haka ba,kukan dake nuna daga ainihin zuciya yake fita ba. Wannan kukan da dukka zuciya da ruhi take yinsa......to mene yafi damunta a ciki?. Tafi maimaita jin maganganun da yayi tsakanin jiya da yau akan abinda Akhnan ke sake shirin aikatawa.......tayi imanin a wannan karon......gagarumin tashin hankali ne ki shirin samun kowa muddin Akhnan wannan karon ta turjewa manufar sultane,batasan kuma iya wa dawa abun zai shafa ba. Ta sani,harda ita a ciki,ita dinma zat cutu,xatafi cutuwa fiye da kowa ma,zatafi cutuwa sama da sultane.......tana cire mammina ne a dukka lissafinta saboda tasan maganar soyayya ko QAUNA tsakaninta da Akhnan wani shiryayyen abune da yake daidai da wasan kwaikwayo,wani shiryayyen abu ne da babu shi sam sam a rayuwa ta badini,sai zahirin da ya kasance idanu ne kadai suke iya ganinsa. "Falaak" Momma ta kira sunanta jikinta da dukka muryarta suna sanyaya. Idanunta da suka kada suka sauya launi ta daga tana duban momma. "Me yafi damunki ne haka?......" ".....momma yaji fa". Ta amsawa morsa safiyya ba tare data sauka daga tambayar ba. Idanu ta xubawa falaak din,har sai da falaak ta zargi wani abu data hanga cikin idanuwan morsa din,sai ta janye dubanta momma din tana sauke ajiyar zuciya. "Ya zama malaminku ne bayan aminta da nutsuwa da tarin ilimin da yake dashi,cikakkiyar kamala da haibarsa da take nuna zallar kamewarsa.......ko ba dade ko ba jima,anjima yanzu gobe ko jibi dole zai iya tsintsar halayyar Akhnan......wannan din baikai ya zama wani abu me tayar da hankali sosai ba..........babban abun tashin hankalin shine bijirewa sultane da tayi a karo na qarshe......a dama ta qarshe daya bata. Biftu nada tsananin taurin kai da kafiya.......bansan wani abu da zai sanya ta janye daga tsaiwar da tayi ba akan ra'ayinta......yayin da shima sultane yake kasancewa tsayayye akan ra'ayinsa a duk sanda yazo kan mataki da gaba irin wannan" Ta qarashe maganar tana jin wani irin zugi na tasowa daga qasan zuciyarta.......wani sashe na zuciyarta kuma na gaya mata a hankali MAMMINA TAYI NASARA........TA SOMA CIKA MURADANTA kamar yadda a tsare a kuma rubuce cikin qudure qudirenta. Saidai wani abu guda daya daya kasa wanzar da rauninsa a kanta shine.......bata yarda bata kuma taba aminta sam sam zuciyarta ta kissima mata WANI MAQIYI.....WANI ABOKIN GABA ko wani mafaraucin lamuranta wai yayi nasara a kanta......wannan yana daya daga cikin QARFINTA da har abada take dogare dashi. ".......jin da sheikh yayi bai kamata ya shiga cikin damuwoyinki ba......damuwarki shine yaya 'yar uwarki zata kubuta?,yaya zata tsira daga dukkan tarakuna......ta yaya zaku taro mutuncin mahaifinku da yake tambal tambal?" Morsa ta qarashe maganan tana duban falaak da dukkan hankalinta. *AKHNAN* Tun daga sanda ta iso qofar farko na sassan mammina.......dukkan wani hadimi dake numfashi cikin sashen ya shiga nutsuwarsa. Masu kaiwa da kawowa da sunan ayyuka dukkaninsu suka dakata da abinda sukeyi,suka kuma tsaya cak a inda suke kawunansu a qasa ba tare da sun iya daga kai sun kalli akhnan ba da yau muryarta ta zama wata abar ga kowa. Wannan lallausar muryar da ake tattalinta......wannan jaririyar muryar da ake yangar furta kowanne irin lafazi da ita......wannan lallausar muryar dake cike da wani irin taushi yanga yauqi da izza......muryar da ba kowa bane ya saba jinta ba......amma a yau da ita take taka kowanne gurbi na sassan mammina tana qwala mata kira. Duk da cewa sunga fitarta,duk da cewa sunsan bata nan,amma kowa ya gaza furta mata hakan. Dukkaninsu cikin shakku da fargaba suke a tsaitsaye,harta gama duba inda ya kamata taga mammina din bata ganta ba,ta fara saukowa da sassarfa sai sukayi kacibus da aisa. "Mammina bata nan ai.......ta fita" Aisa wadda buhaina ta rarrafa ta kirata don ita daya suke sanyan ran zata iya controlling Akhnan din ta fada tana dubanta tare da qoqarin nazartarta. Dukka hannayenta biyu Akhnan din ta yarfar,tana jin wani abu yana mata yawo tsakiyar kanta. "Me yasa mammina zatayimin haka?,me yasa zata fita a daidai sanda nafi buqatar ta?" "Kina da momma ai.....morsa safiyya tana nan" Aisa ta fadi cikin bawa Akhnan qwarin gwiwa. Maganar aisan daidai take da zubawa wuta fetur,daga blue eyes dinta tayi ta zubewa aisa din su,sai kuma ta tuna dole dole akwai wanda take buqata,ko yaya tana buqatar wani on her side. Takowa tayi ta kama hannuwan aisa duk biyun. "Don Allah aisa.....S'ilvouse plâit........zaki rakani gurin sultane?" A mamakance aisa take kallonta. "Gurin sultane kuma?,biftu a irin wannan lokacin......" Kai ta gyada mata tana qoqarin calming kanta. "Dole naga sultane aisa......ina buqatar hakan". Hannunta daya aisa ta zame ta dora yatsarta a qirji. "Ni kikeso na rakaki gurin sultane ki gaya masa kin watsar da zabinsa?......kin wofantar da zabinsa?.....zabin nannie?". A hankali Akhnan ta ware ido tana duban aisa. Zabin nanny?,me hakan yake nufi?,bayan sultane harda nanny ma saida morsa safiyya ta hada?,bayan sultane harda nanny saida morsa safiyya ta shiga tsakani?,sai da tasan cewa tabbas ta gindaya wani abu a tsakaninsu?. A yaushe?,a kuma wanne lokaci hakeem ya zama zabin nanny?. Kai take girgizawa da sauri.....da gaske wannan yaqin yakeso ya cita......da qarfinsa ya tunkarota.......dole itama ta cire kowanne irin tsoro daga ranta,ta tunkari kowa......ta tunkari komai......ta kuma tabbatar da cewa mafarkinta burikanta.....ra'ayinta dama muradinta dukka babu guda daya daya rushe a ciki. Hannun aisa ta saki,taja da baya a hankali tana duban aisa,sannan ta juya tana takawa da dan sassarfa. "Akhnan!......biftu!" Aisa tayi kiranta da sauri tana daga hannunta tamkar zata kamota. Mamaki da tsoro ya cika zuciyar aisa........tana kokwanto da shakka da kuma jin d'ar d'ar din kada fa da gaske akhnan sultane zata tunkara?,kada ya zamana da gaske zata je garesa ne ta tabbatar masa hakeem ba zabinta bane. *HAISAM* Cikin kebantattun mintunan da suka shafe da sultane wani kima da martabarsa ya dinga ji yana daguwa a ransa. Wani girma irin na UBA yakejin yana bashi. Mutum ne da ya fifita lahirarsa akan duniyarsa.......qabarinsa da aljannarsa akan mulkinsa. Ta wanu fuskar sai yake kallon kamar motii abba jifar ne a gabansa,wasu lafuzzansa.......da wasu daga cikin kalamansa kamar dai motii. Wani sashe kuma na zuciyar haisam yana tabuwa da tausayin sultane kadan kadan sanda yake fadin. "Zaka iyayimin alfarmar zamemin D'A,ka kalleni da idanun da kowanne d'a yake kallon ubansa........ka zama mashawarcina makusanci kamar yadda kowanne d'a yake da ubansa?". Shuru yayi yana sunkuyar da kansa qasa cikin girmamawa,kafin a hankali ya saki numfashi. "Umarni ne daga Allah S A W cewa,haqqine a wuyan kowanne musulmi idan an nema shawara ya bayar.....zanyi dukkan iya abinda iko ya bani,zanyi kuma daidai gwargwadon ikon da bai shallake iyawata ko hankali ba" Kai sultane ya gyada a hankali,murmushin nutsuwa na bayyana a fuskarsa. Sake gamsuwa yakeji yana yi da haisam din har a yanzun da yake zaune a gabansa. Tun daga wancan ranar daya fara sanyashi cikin idanunsa yakejin kamar ba ranar ce ranar farko daya taba saninsa ba cikin rayuwarsa. "Allah yayi maka albarka.......ya kuma albarkaci iyayen da suka samar dakai......zanso in sansu.....zanso sanin iyayen da suka ci nasarar mallakar kadara me tsada irin wannan,diyan qwarai din da yake tamkar haske cikin duhu". Sosai maganganun sultane suka sauka saman zuciyarsa......kalamansa na buqatar sanin iyayensa sukayi kyakkyawan masauki a zuciyarsa. Bai shiryawa wannan ba.......hasalima baizo agadez domin zama ba. Aiki ne ya kawoshi,aikin kuma da ya gama lissafinsa cikin duk wani tsare tsarensa,iya wuyarsa dadewarsa ko nauyin aikin ya cinye watanni uku.......ya bawa kansa tabbaci zaburarwa da horon da yayi yaqinin bazai wuce watanni uku ba ya zaqulo wanda yazo nema,don haka baiga muhallin da zai bar wani alama ko gurbi cikin masarauta da zasu san wayeshi ba.....a cikin aikinsa ko kuma bayan ya kammala. "Daga yanzu......kuma daga yau kana da cikakken ikon shiga kowanne guri shiyya ko muhallin da jinina je kadai suke da wannan.....daga yau kana da matsayi cikin masarautar agadez daidai da data CIKAKKEN D'AN SULTANE MUHAMMAD HAMMUD...sannan kuma ina meyi maka tayin dawowa cikin masarauta ka rayu a cikinta,bisa kyautar gida a cikinta da zaka rayu iya adadin yadda kakeso". Zamansa ya gyara cikin girmamawa,yana jin akwai abubuwa daya kamata ya gyarasu tun a yanzun,tafiyarsu a haka zasu iya taba aikinsa. "Ina godiya qwarai da gaske da dukkan karramawa martabawa da kuma karamci......na karbi dukkan komai daga gareka......batun gida shima na karba,saidai dawowar da zama a cikinsa zai dan bani wahala haka lokaci guda,zanyi qoqarin daidaita abun daidai da yadda jikina da zuciyata zasu saba". Murmushi sultane ya qara saki,yana sake jin dadi,bai taba tunanin komai zaizo masa da sauqi haka ba,bai taba tunanin samun makusanci haka me debe masa damuwa a kurkusa irin haka ba. "Kada ka damu,kayi komai a hankali yadda zai dace da ra'ayinka" "Na gode......zan iya tafiya?". " Zaka iya,Allah yashi albarka" Sultane ya fadi sannan ya miqe da kansa ya masa tattaki har zuwa bakin qofar dakin ganawa da baqinsa na musamman,haisam din ya taka a nutse ya fice,sultane kuma ya juya zuwa ciki yana jin yadda zuciyarsa ta cika da wani irin sanyi da nutsuwar daya jima bai samu irinta ba. Ba kasafai nutsuwa kan bar jikinsa ba komai girman abinda ya tunkaroshi. Mafi yawan lokuta yakan sanya hankalinsa da nutsuwarsa gaba da komai da zaya faru komai girman wannan qalubalen. Sassanyar iskar hadarin farkon damina dake kadawa a kebantaccen sassan sultane muhammad ke ratsa wani sashe na jikinsa,yake sake wanke masa qofofin zuciyarsa da dukkan wata mahada ta tunaninsa da kan kaishi zuwa ga dogon nazarin da yakan shiga lokaci zuwa lokaci. Fuskar nan dake dauke da cikakkiyar kamala da nutsuwa a dinke tsaf,ba wani digon fara'a saboda tunanuka da suka cunkushe masa kai masu yawan gaske. Wasu suna hawa wasu suna sauka,yana qoqarin ture wasu yayin da yake qoqarin yiwa wasu muhallin da zasu zauna sosai kan mizanin awonsa ba tare da girgidi ko rawa ba. 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 64 Cikin jikinsa yakeji lokaci yayi,lokaci yayi daya kamata ya qarawa aikinsa himma.......ya qarawa aikinsa gudu,ya kuma qarawa aikinsa energy don tabbatuwar kammaluwar aikin cikin watanni ukun daya qididdige tun a farkon lissafinsa. Kamar gilmawar kibiya ya hangi giftawar mutum,sanye da irin wadannan tufafin.....wadannan kayan daya jima yana nazarin a inda idanunsa da zuciyarsa suka taba saninsu. A ranar da yaga wannan motar.....motar da ya tabbatar daga cikinta yaji sautin yaren OROMO na fita daga cikinta,yaga kuma gilmawar mutum sanye da irin wannan tufafin. A sanda hankalinsa ya dauko ga son iya gane wadda ke sanye da kayan,a sannan ya sake ganin wata sanye da irin tufafin,sai lissafinsa ya soma komawa baya,cikin qasa da second biyar kwanyarsa ta harba BA LAUNIN SUTURAR MACE DAYA BANE sautin ya buga cikin kansa,sai ya lumshe idonsa ya kuma zuqi numfashi,numfashin da baikai ga saukeshi ba idanunsa suka dauko masa hotonta tana dab da shi,da nisan tazarar da baikai koda taku guda a tsakaninsu ba.......kafin kuma kwanyarsa ta gama tantance masa komai.......kafin tunaninsa ya gama gaya masa abinda ya dace yayi......kafin wannan kuzarin da wannan zafin naman yayi aiki yadda ya saba yi masa ta daki faffadan qirjinsa da dukkan jikinta,wannan ya sanya ta koma da baya kaman an hankadata zata fadi.....faduwar kuma da ya tabbatar idan tayi ta munanan raunuka zata samu saboda shimfidaddun qananun duwatsun dake a wajen,tilas ya miqa hannusa da wani irin zafin nama ya riqo nata hannun,tafukan hannuwansu suka gauraya dana juna,abinda ya tsaida bugun zuciyarta na wasu daqiqu,ta kuma daga blue eyes dinta da a dazun ta zubesu kan duwatsun tana wassafa yadda suka daki bayan kanta ta maidasu kan wanda take tunanin ya dakatar da ita daga faduwa. Tsaf idanunta suka sauka daidai cikin wadannan rusunannun idanuwan.......wadannan idanun da idan ya rusunar dasu zaka dauka irin idanun mutumin da bacci ko gajiya suka yiwa mugun kamu ne. Tun daga cikin qwayar idanunta har zuwa tafukan hannunta zuwa tafin qarqashin qafarta taji wani irin abu,wani irin yanayi......wani irin magnet me qarfin gaske gauraye da qaqqarfar faduwar gaba da taji tana barazanar tsinko zuciyarta daga qirjinta......wannan feelings din kuma ya gauraya da wani irin matsanancin tsoro cikin second guda kacal jin yadda ya zame hannunsa daga nata ya saketa ta tafi zata fadi a inda take tsoron faduwar,Allah ya taimaketa ta dafe hannunta guda daya wanda saida taji ya amsa. Tsananin mamaki da wani irin abu da taji yana zagayawa a jininta ya hanata daga kai ta kalli wanda yayi mata wannan danyen aikin?. Wayeshi cikin masarautar agadez gaba daya?.....me yake taqama dashi?. Ya sanya hannunshi cikin nata......ya kuma saketa har ta kusa kaiwa qasa......sannan kuma a hankali taji wani calm sound yana furta. "Astagfirullah" Fusatattun idanunta ta sake dagawa zata dubeshi,daidai sannan ta tsinci yana yarfar da hannun daya riqe mata hannu dashi,ya kuma saka daya hannun yana maida rawaninsa daya sauke kadan,yana qarasa rufe bakinsa zuwa hancinsa........take yanayin daxun ya dawo mata. Irin wadannan idanuwan da take gani sak a mafarki ne.....wannan idanun da suka zame mata barazana......idanun mutumin mafarkinta.....mahayin dokinta,abokin tserenta,abokin gasarta,abokin adawarta.......mutumin da TAFI TSANA DUK DUNIYA......Mutumin da qiyayyar morsa safiyya a ranta ma saidai ta biyo bayan tashi. Miqewa tayi a matuqar fusace,saidai kafin ta samu daman cewa komai har ya bada tazara daga inda take,sai wannan qamshin da har yanxu ba zata iya mantawa dashi ba.......wannan qamshin da ta taba ji a wancan ranar......a hippodrome Niamey....qamshin da taji a jikin wancan mutumin da a yanzun take sake jinsa. Wannan qamshin da aqalla a sirrance ta sanya an kawo mata kalar turaruka daga qasashe daban daban da manyan riders na dawakai na kowacce qasa sukafi using nashi......a qalla sama da kwalba dari bakwai.......saidai ko me kama da wannan qamshin bata samu ba........ya akayi shi wannan da bata san waye ba ya samu qamshin?. Daukuwa hankalinta yayi,ta sake shaqar iskar da kyau tana fesar da ita gami da lumshe idanunta. Ganin sultane a yanxu yana da matuqar muhimmanci......kamar yadda sanin waye wannan mutumin me tsananin tsaurin ido........karbar kalar turaren da yake amfani dashi bayan tasa an ladabtar mata dashi akan abinda ya aikata din a yanzu. Maida dubanta tayi ga inda take tsaye.....ba guri bane na wasa,ba kuma guri bane da kowa da kowa yake da damar takowa xuwa ciki ba,don koda masu tsaron gurin suna ta wajen gurinne bata cikin gurin ba. Dukkan wanda ka gani yana kai kawo a gurin tabbas yana cikin AHALI ko jinin sultane,kusanci kuma bana wasa ba. TO WAYE?.......KO ALJANI NE?. Wani tsinkewa zuciyarta tayi,idanunsa irin idanun nan da take gani a mafarki ne,irin wadanda ta gani a hippodrome ne sak!....wasu iri idanu haduwarsu da nata a jikinta takejin ba gama garin idanu bane.....kamar su din an cirosu daga cikin wani abu na dabanne bawai daga nau'inkan idanuwan mutane data sani ba......qamshin sa.....dama abinda ya faru a yanzun,komai kamar ya maimaita kansa ne. Wani irin sanyi qafafunta taji sunyi,tsoro taji ya shigeta,ga yanayin gurin daya soma lullumewa saboda gabatowar magariba. Me zai faru idan ya zamana aljanu sun fara wasa da hankalinta ne da tunaninta?. Tafin hannunta takai saman fuskarta da niyyar shafa don bawa kanta relief,saidai kuma wannan qamshin dai taji fes cikin hannuwan nata kamar an diga mata turaren ne a cikin su. Da sauri ta janye hannun tana duban tsakiyar tafin hannun. Hannun dai nata ne,wannan lallausan tafin hannun da kowacce rana cikin wankeshi ake da nau'ikan mayukan wanke hannu,ta kuma shafeshi da ajiyayyen cream na musamman saboda hannun kawai,amma qamshin nasa ne......qamshinsa ne. "Kina dab da rasa ganin sultane" Wata zuciyar ta yunquro mata da lamarin da ya sanyata takowa ganin sultane kai tsaye ba neman izini ba iso. Damqe tafin hannun nata tayi tana jin cewa wannan shine issue na gaba mafi muhimmanci a gareta. Ta tsani wanzuwar qamshin a tare da ita......amma a yanzun tana buqatarsa a hannunta zuwa awannin da zata kammala ganawa da sultane. Tun a parlor din farko data hangi sultane din tsaye kowanne karsashi nata ya soma sulalewa. Wannan kwarjinin dake lullube da fuskarsa dama gangar jikinsa gaba daya suka soma dakushe nata kwarjinin dama jarumtarta,sai wani irin rauni ya fara sauko mata,irin raunin da d'a kanji a sanda yake neman alfarmar da ba wanda zaiyi masa shi sai iyaye,sai kuzarinta ya ragu,tayi qasa da kanta tana takowa zuwa gabansa,ta iso dab dashi sannan ta sulale saman gwiwarta tana kafe gwiwoyinta a qasa. Wani abu qwaya daya da duk duniya sultane keda wannan girman da zatayi masa shi......wani aiki da a duniya banda mahaliccinta babu wata halitta data taba zubewa hakan a gabanta,sai ta saki siririn kukan da bata taba yarda ta yishi gaban kowa sai gaban mutum biyu SULTANE DA MAMMINA. Don koda cikin addu'a da salla batasan yadda ake kuka ba,bata zama doguwar addu'a saboda bata taba hasashen tana da wata buqata ba. Rayuwarta ta cike mata tako ina cif cif a nata idanun,bata da sauran abinda zata kuma roqa,rabbana Aatina fiddunya hasanatan wafil Aakhirati hasanatan wa qina azabannar kadai take iya maimaitawa. Yana tsaye kawai goye da hannuwansa a qirji. Baice mata ci kanki ba,kaman yadda baice ta tafasa sauke ba. Indai akhnan ce......indai khadeejatu ce,indai kuma shine ya haifeta yasan tabbas zatazo. Ya shiryawa zuwan nata kuwa da kyau,ya kuma shiryawa ko meye zata ce,ya riga ya yanke hukuncin da ba abinda zai sanyashi maida hannun agogo baya. Lokacin aurar da AKHNAN daga masarautar agadez yana ji a jikinsa yayi,babu kuma abinda zai sauya wannan. To amma ta wani Fannin.....idan har yace kukanta baya taba ranshi......ko kuma kukanta bata mintsinin zuciyarsa yayi qarya. Kowanne iyaye akwai cikin 'ya'ya wanda Allah yake jarrabarsu dashi,shi kam ya amince da akhnan din aka jarabceshi. Baya iya dauke idanu daga dukkan wani ko wani abu da zai kusata da ita ya illatata ko ya cutar da ita.....bashi da juriya jumuri ko jarumta game da ita.....ba kuma wai haka kawai ta samu dukkan wadannan ba....Aah SAFEENA ce sila. A duniyarsa ba wata halitta sama data safeena......ba wani mutum a jiya ko a yau shekaran jiya ko gobe da zai iya wafce matsayin safeena a rayuwarsa,har zuwa ranar da numfashinsa zaibar gangar jikinsa. "Inda zaki sauqaqawa kanki khadeeja ki tashi hakanan,don babu abinda zai sauya wannan hukuncin......ZARTACCEN ABU NE kuma tabbatacce da ikon Allah......ban taba tunanin akwai lokaci da zaizo da zan iya zartar da haka ba a kanki......sai gashi yanayi yazo da bayanan da suke gwada hakan shine gata na qarshe da zan gwadawa rayuwarki......ki tafi ki fara shirye shirye......na baki watanni biyu kacal ki horas da kanki yadda zaki zauna da HAKEEM a mazaunin mijin aurenki na dindindin". Ya qarasa maganar yana soma barin wajen bayan ya dauki carbinsa da alkyabbarsa ya maida saman plain jallabiyyar jikinsa. Tafi kowa sanin sultane bawai don tafi kowa doguwar rayuwa dashi ba......tafi kowa saninsa domin shi din jinin jikinta ne. Daga yadda ya nuna mata ta sake karaya da samun tabbacin hukuncin sultane na wannan karon BABU GUDU BABU JA DA BAYA!. Indai hakan ta kasance ta cika marar nasara.....tozartacciyar da zata auri namijin da yafi kowanne nau'in mazaje rauni da kuma rashin NASARA. Namiji me ilimin arabiyya kadai?......koda yana da ilimin nasaara ba zabinta bane,hakeem da ire irensa dukka sun kasa .....namiji irin hakeem koda aisa ko shehnaz bare falaak ba zata yiwa fata ba. Koda tana ra'ayi muradi ko burin aure......tsayayyen namiji.....jan zaki.....me budaddun idanun da suke iya hangen duniya a tafukan hannuwansa.......me iya sarrafa tunani dama abinda duniya ke ciki.....me idanu a kowanne fanni na rayuwa,gwarzo jarumin da ba abinda ke iya raunanar da zarrarsa......irin wannan ne WATAQILA......WATAQIL ta iya bashi dama cikin kaso daya cikin dari ya gwada sa'arsa.....sa'ar da idan ta tabbata wala'alla ta bashi daman ci gaba da nemanta har zuwa sanda zata iya jin cewa ita KHADEEJA MUHAMMAD HAMMUD zata iyayin aure a rayuwarta. Sanda takai qarshen tunaninta sultane ya dade da bacewa ganinta. A hankali yakai yatsarta kan fuskarta tana taba dumin da taji yana gangaro mata. Duban yatsun ta sakeyi,hawaye ne......farare tas masu dumin da batasan sun sauko mata ba. Kuka ba dabi'arta bace......amma akan sultane da hukuncinsa zata iyayin sama da kuka dinma. ★ "Me yasa ka nuna masa kana iya zama a gidan nan gaba?". Omari da ya zuba masa idanu yayi tambayar ga haisam din kai tsaye. A hankali ya bude idanuwansa,duk da cewa bai motsa ba ko kadan daga yanayin yadda yayi relaxing cikin kujerar. A nutse yake duban omari,yana kuma son hotonta ya bace bat daga idanunsa. Muryarsa can qasa,cike da gajiyar da yake ji cikin sassan jikinsa yace. "A wannan karon...cikin jikina nakeji akwai wani abu cikin masarautar,da akwai wani abu cikin gidan,jikina ne kawai yake bani hakan,ba don ina da tabbaci ba.....komawata bata lokaci daya bace.....komawata zata zama kadan kadan ne har izuwa wani lokaci idan komawar ta tabbata gaba daya.......naji oromian language a muhallin da naga gilmawar tufafin hadiman cikin gidan.....tabbas dole yana kasancewa akwai alaqa ko sanayya ta juna tsakanin duk mutumin da kuke yare daya dashi.... Qabila daya a sanda kuka tsinci kanku a wata baquwar qasar da ba taku ba.... Tabbas akwai wannan zumuntar" Ya qarasa maganar yana jin tabbaci har cikin ransa. Shuru omari yayi yana jinjina kai,hasashe da maganganun haisam a bisa layi suke,baisan dalili ba,amma shima a jikinsa yake jin kamar nasara ce take tunkarosu. "Meye sunan yarinyar da ka hadani race da ita?". Haisam yayi tambayar sanda yake miqewa tsaye,sanye da wata fara qal din shirt cotton sosai me gajeran hannu da round neck,abinda ya bayyana cikakkun muscles dinsa da suke gayawa duk wanda ya kalla yanayin qarfi da yawan motsa jikin da yake dashi. Hannunsa zube a aljihun wandonsa da bai sauka har qasa ba. 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 65 Daga kai omari yayi yana dubansa yana kuma d'an jin mamakin tambayar,don ko a wancan karon haisam din baima tsaya sauraren kowanne bayani akan race din ba,abinda yafi maida hankali kawai shine yadda wasan zai qare,su kuma samu daman shigewa cikin agadez a sirrance. "Princess akhnan muhammad hammud.......qasaitacciyar d'iyar sarki muhammad hammud......bansan ya zata kasance ba duk ranar da tasan cewa kaine silar faduwar nasararta" Omari yayi maganar yana sakin murmushi idanunsa akan haisam. Ya san halin haisam din,yana da sauqin kai ta bangarori da dama.... Yana da bala'in bada girma daraja da martabawa ga dukkan wanda yake sama da shekarunsa........amma fa bashi da dadi a wasu lokutan......yana da wata irin zuciya da muddin aka tabota......sauketa yana zama abu me wahala......ba kowanne irin hali da dabi'u yake tolerating daga waninsa ba......akwai wasu halaye da dabi'u da muddin kana dasu kada kayi kuskuren sha'awar yin rayuwa dashi. Yana da girmamawa don haka bayason raini,bai fiya daukan kansa da girma ba......amma kuma baya daukan raini wulaqanci ko qasqanci. Yana da dokoki......yana da iyakoki.......yana da layuka da yakam shata akan kowanne mutum da zaiyi rayuwa dashi. RESPECT wani abu ne muhimmanci a tare dashi........baya wasa dashi baya yiwa wani wasa da mutuncinsa. Miskili ne irin miskilancin da idan ya motsa masa zaka jima kana rayuwa dashi baka gama fahimtar ya sound na muryarsa yake ba. Zai iya wuni guda kuna hira yana maqale da littafi abinsa,ko kunnensa ba zaku samu ba ballantana hankalinsa. Murmushi yafi zame masa amsa akan ya furta da bakinsa,dariyarsa tana da qaranci qwarai da ba kowa yasan launinta ba.......saidai duk da wadannan yana da zuciya me taushi......yana da wani irin kyakyawar zuciya me cike da dimbin alkhairi..... Irin alkhairin nan me sanyi da saka zuciya a mamakin mallakin zuciya me tarin alkhairi irin wannan. "Na fahimci abubuwa da dama a tattare da ita a fitata da nakeyi cikin mutanen ta" Omari ya dora da fadi ganin ya samu daman hiran da yakeso yayi da haisam din. Taku biyu haisam din ya qarayi gaba,abinda ya tabbatarwa omari idan bai hanzarta ba haisam yana iya tafiya abinsa. "Bata yana faduwa ba a dukkan komai.......itace gaba a kowanne abu da zai taso,ta tsani faduwa.......tana da wata irin izza da take rayuwa sama da izzar da sultane mahaifinta yake da ita. Ba kowa bane yasan fuskarta,ba kowa bane yasan muryarta,ba kuma kowa bane yasan ainihin kamanninta koda kuwa wadanda suke rayuwa cikin gidan.......a cewarsu har yanzu ba'a halicci mijinta.....su a karan kansu sunsan babu wata halitta data dace da princess akhnan hammud..........kaima kuma tana neman dukkan wata hanya da zata sake tsere da kai.....hakan kuma nasan baya rasa nasaba da faduwarta daka zama sila" Omari yakai qarshe yana miqa masa wayarsa bayan ya bude wani abu yana miqa masa. Taku biyu haisam yayi ya dawo baya,ya kalli wayar da lumsassun manyan idanunsa kafin ya miqa hannu ya karba yana dubawa. Har yanzu murmushi ne shimfide saman fuskar omari,ya dade yana neman wannan damar da zaiwa haisam magana........yanason yaga dambarwar ya zata kaya. Yana ganin yawan saqonni daga hippodrome suna neman cikakken bayanai a kansa,da kuma yawan adadin request da suke sake turawa na shirya sabon race da zai zama globally gaba daya. Zayaso yaga yadda nasu prince din zai sake nunawa wannan qaramar gimbiyar TAZARA da bambamcin dake tsakanin MAZAN ETHIOPIA da matan AGADEZ. Yayi imanin cewa koda sau million nawa ne zata sake gwabza tsere da haisam,abune me wahalan gaske taci nasara a kansa. Baisan gaibu ba......amma ta bangaren sarrafa dawakai da raqumma baya tunanin har yau akwai mutumin da yakai haisam fasahar sarrafasu. Bai manta dalilin hanashi wasan tseren da akan shiryawa 'ya'yan sarakai da 'yan sarauta na cikin yankin jimma gaba daya ba....... Qwarewarsa da zarrarsa tafi ta kowa,shi kadai yake zuwa na daya a dukka shekara ko watannin da za'a shirya wasan,dole nanay ta sanya aka janyeshi daga komai gudan bakin al'umma. Email din farko kawai ya karanta......tun sakannin da suka gilma tsakaninsa da ita a jiya yaji a jikinsa itace. Yana da wani kaifin basira da fikirar laqantar abu. Second biyar din kacal suka dawo masa da abinda ya faru a wandancan mintunan na satittikan baya. Wannan abun da yaji ya tsarga jikinsa ya gauraya da jininsa me kama da jan wutar lantarki still shi ya sake ji a dukka jijiyoyin jikinsa dake aika jini. Idan ka dauke mahaifiyarsa nanay......rumaisa noory da Anani da suke shaqiqansa.......ba wata mace a kaf rayuwarsa da tafukan hannunsu suka taba gauraya da juna. Ita ta fara kafa wannan tarihin da hakan ya faru a tsakaninsu har sau biyu,wanda yakejin nauyin zunubin haka saman kowanne tafi na hannunsa har yanzu. Sanda suke makaranta.......rayuwar makaranta rayuwa ce dake cakude da tarin nau'ikan mutane mabanbanta. Duk kuwa da cewa sunyi karatu ne cikin larabawa,sai suke ganin larabawan zamani,ba asalin balaraben mutum me tsananin kamun kai da sanin addini ba. Shagalallu da har shagalarsu takan basu mamaki. Yana da wani irin haiba da daukan hankali,wanda sassanyan kyau da wasu kebantattun halitta da Allah ya bashi ya qara yawan adadin matan dake da muradi a kansa. Daure fuskarsa......janye jikinsa daga shiga dukkan wasu huldodi da mu'amaloli da suka shafi Mata a ciki basu sanya hakan matan sun janye jikinsu daga neman alaqa dashi ba......saima qara neman shiga da sukeyi. Kamun kannasa sai ya sake zame masa wani irin ado me fusgar hankuls,ba ga ashararan 'yammata ba,harda kamammu masu kunya da kintsi......a lokacin da gaba daya baisan wani abun burgewa tattare da d'iya mace ba,bai tantance wani abun jan hankali ba akan diya mace ballantana yaja hankalinsa. Abu daya ya sani.....mace me suturce jikinta,mace me kunya yana ganin martabarta kima da mutuncinta fiye da me bayyana tsiraicinta. Karatu yayi masa wani irin mugun kamun da bayajin zai iya hada space dinsa dana tunanin wata diya mace......ya samu wani babban gurbi a rayuwarsa da baya tunanin akwai sauran gurbin wata mace. Duk da cewa yana cikin shekarun da jini ke harbawa a jikinsa da sauri,yake kuma aika saqo izuwa zuciya kwanya da ruhi. Yana ganin yadda a hankali su mutallab wannan feeling din nason yin budurwa.......wannan feeling din na nemewa zuciya abokiyar hadi kuma abokiyar tarayya sannan abokiyar rayuwa ya fara tasiri a kansu. Ko kadan bai zargesu ba,don yasan sunkai wadannan shekarun,don shi bai tasirantu da wannan ba ba lallai ma kowa ya zama haka ba,bugu da qari dukkaninsu kamar guri daya aka musu tarbiyya. SARAUTA sunan da aka bawa 'yan team dinsu cikin makarantar kenan da harshen hausa. Kyau kwanya da gata dukkaninsu Allah ya musu baiwa,saidai wani yafi wani. Su biyu ne 'ya'yan da suka fita daga gidan sarauta cikin team din nasu,wannan ya sanya sukayi representing sunan team din,don shi da maleek din yanayin gadon sarauta da sukayi sai suka sake zama yanayinsu daban,ba kuma wai don sun qirqiri hakan bane a karan kansu....a'ah,wani yanayi ne dake bibiyar jini. Dukka bayanan omari yake saurara sanda yake qoqarin maida email din kan nashi wayar,ya kuma saukeshi daga wayar omari din sannan ya miqa masa wayarsa,bai kuma tsaya qarasa jin qarshen labarin ba ya soma takawa yana fita a parlor din. Wanka yakeso yayi da ruwa me zafi kafin ya kwanta,sannan kuma ya kira nanay da yakejin kewarta. Kewarta dukka da kewar gida yakeji,kaman yadda yasan zuwa yanzu qannensa dukkaninsu sunyi kewarsa,idan ma akwai wanda yakejin ko a jikinsa hussam ne,zaima ji dadi me matsa mishi ya kauce ya bashi guri,zaici karensa babu babbaka. Sanda ruwan me dumi sosai ya soma ratsa gabbansa sai ya saki wata ajiyar zuciya yana nutsewa cikin bathtub din sosai. Haka kawai komai nata yake dawo masa,wanda duk yadda yakai ga ture tunanin sai daya mamaye ilahirin kwanyarsa. Abinda ya faru akan kunnensa.......maganganun omari da bayanansa.....email din da aketa turawa da komai da komai,take yaji wani bacin rai yana sauka saman zuciyarsa a hankali. Tana da izza tana kuma buqatarta.......tana son girmamawa daukaka da martabawa amma bata iya aiwatar da ita akan kowanne d'an adam. Ta iya duban idanun dukka wanda taso ta tozartashi da kalaman da dukka sukazo bakinta,batasan me ake nufi da MUTUNTAWA da KARRAMA DAN ADAM ba....... Masanan ilimi sune halittar da tafi RAINAWA tafi TSANA mafiya kuma qasqanci a idanunta......while kuma sultane mahaifinta ya kasance mutum me karrama wannan nau'in mutanen da ita kuma suka kasance wulaqa tattu a idanunta......garin yaya RAYAYYE ya haifo MATACCE?. Daga ina ta samu dukkan wadannan baqaqen halayen da suke kishiyoyin juna da halayen mahaifinta?.......mahaifiya?. Ya tambayi kansa tunaninsa yana tsayawa cak!. Qin aminta da hakan yaji zuciyarsa tayi,indai wannan mahaifiyar ce.......wannan dai mahaifiyar data yi aike cikin girmamawa da karramawa.......tayi aike cikin bashi dukkan cikakkiyar dama......cikin neman alfarma da qasqantar da kai daga dukkan girman da sarauta ya bata take neman ya zamewa yaranta malami.........indai itace zuciyarsa da ruhinsa basu gamsu ta dauki kowanne dabi'a nata ba!. "Dole akwai daga inda damuwan yake!" Ya fadi a hankali yana bude idanunsa gami da motsa labbansa. "Matan sultane nawa?" Tambayar data tsaye masa a ka kenan,yake jin ya kamata ya sani. Tasiri aikinsa yayi masa sosai cikin rayuwarsa da yakan saurin harbo wasu abubuwan a sanda yake ganin tafiyarsu ba daidai ba. Ya qarasa wankansa a nutse,ya kuma nade jikinsa da babban towel,ya nade sumarsa da wani,sai fuskarshi tayi kyau,kaman wanda yayi hakanne da manufar ado. Kusan komai ya sanya kyau yake masa,duk da shigarsa me sauqi ce amma kuma sutura ce da kowacce zaman kanta takeyi. Tsadarta kadai idan kaji xaka sake kallanta ka qara. Dukka jallabiyarsa daga asalin factory din da mafi yawa suke saqa jubah,cloak robe da jallabiyyar gidan sarautar saudiyya ne. Wata mitsisiyar waya da duka duka batafi tafin hannun qaramin yaro ba ya jawo,ya danna wasu lambobi dake haddace a kansa ya soma kira. Bugu uku aka dauka,muryar maher ta bayyana cikin girmamawa. "Matan aure nawa ne cikin gidan sarautar agadez?". "Biyu ne obbo" Ya amsa masa,saidai kafin ya qara cewa wani abu maher yace. "Morsa safiyya.....da mammina zaituna......morsa itace ta saka oustaz Ousmane ya kawoka a madadinsa,mammina zaituna itace uwargidansa,kuma ita ke riqon shalelensa akhnan,wannan ya sanya matsayinta yake na daban cikin gidan". "Is okay" Ya fadi yana katse maher,don ba wai dogon bayani yake buqata ba. Koda yana da buqatar yana ji zai bincika ne da kansa.........yana sake jin buqatar zama da wanzuwa cikin gidan tun daga sanda zuciyarsa ta ayyana masa wanda yayi yaren oromo yana da alaqa da cikin gidan. Wayar ya janye gefe yana daukan hand drayer don tsane kansa da ita. Basai ya tsawaita tunaninsa ba.......zaiyi wahala daukan dabi'u da ra'ayiyyikanta ta samosu ne daga UWAR RIQONTA?. "zai iya kasancewa" Ya bawa kanshi amsa yana qoqarin cillar da tunanin. Ya gaji da tuna komai da ya shafi gidan sarautar,yana buqatar tuntubar nasa ahalin,yana buqatar jin muryar nanay dinsa,wadda ita daya ke debe masa duk wani gajiya da xaiji daga can cikin kwanyarsa akan aikinsa. ★ 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 66 __________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah __________________________ Kadan kadan murmushi ke fita saman fuskarta ba tare da tasan hakan tana kasancewa ba. Cikin sukuni da saituwar al'murabta take jin kanta,tana hango wasu kwanaki kadan masu zuwa yadda komai zai zo mata da irin tsari da burin da take muradi. Ta sani ta jima tana shan wahala ta zuciya da gangar jiki,tana jin wannan kadai ya isa ubangiji yayi mata alfarmar bude mata kowacce qofa don isa ga sauran muradanta na duniya da suka rage mata. A nutse motar dake lullube da baqaqen glass tinted ta sauka daga hannunta,ta kuma fara kutsawa cikin wani qaramar gona da yafi girman lambu ba tare da damuwa da adadin shukokin da take takewa ba,don dama bawai anyi shukokin bane don su amfani kansu kosu amfani wasu ba,ba kuma an dasa su sun kuma girma bane don suci gaba da rayuwa irin rayuwar da kowacce shuka keyi don isa ga wani mataki ko kuma muradi. Tafiyar mintuna goma kacal motar ta fita daga cikin shukokin,wani dan madadaicin fili ya bayyana a gabanta,wanda wani plate house ne daga tsakiyar filin,qawatacce da wata irin qofa me kyan gaske. Matuqin baiyi koda horna ba gate din ya bude qaramar farfajiyar gidan ta bayyana,motar kuma ta kutsa kai zuwa cikin gidan,ta tsaya daga tsakiya,sannan mutum daya cikin mutane ukun dake tsaye a gurin suka qaraso da sassarfa da kuma tsananin girmamawa suka bude hannun da mammina ke zaune. A qasaice ta sauko,wanda kafin qafafunta su qarasa direwa a qasa ta saki tamabayar. "Ina tamim yake?". "Bai qaraso ba" Suka amsa mata cikin matsanancin girmamawa suna sauke kawunansu a qasa. "Muje na ganshi" Ta basu umarni na kai tsaye,wanda tana sauke maganar sukayi gaba da hanzari suna mata jagora. Qawataccen parlor ne da aka zuba wadansu irin kayan alatu da sam bana qasar bane ba,wasu irin kayan alatu masu daukan hankali da nuna asalin tsadarsu da nauyin kudin da aka kashe domin siyansu. Gaba daya daga cikinsu yayi zuwa daya daga cikin rufaffun qofofun da suke kulle,mammmina ta bishi a baya,har zuwa sanda ya murda dakin ya tura ya budewa mammina yana tsayawa daga gefe alamun bata daman shiga. "Bacci yakeyi?" Ta jefa tambaya ga mutumin da yake tsaye din kansa a qasa. Tambayar tata da alama baiso ta fada a kansa ba,ko kuma baiso ta ruskeshi ba,don hannunsa ya aza saman kansa yana shafawa a nutse. "A'ah......yadan sha......" "Sake bashi kukayi?!" Ta furta a tsawace cikin wata irin fusatacciyar murya data haifar da shuru cikin falon. Ba wanda ya iya motsawa ko ya amsa a cikin su,sai sadda kawunansu da sukayi a qasa. "Sau nawa zan gaya muku?.......sau nawa zan maimaita muku?" Ta sake musu tambayar da duk cikinsu ba wanda keda amsarta. Itama ta fahimci babu me iya bata amsa,don haka ta taka da hanzari tana cusa kai cikin dakin. Yalwataccen daki ne da aka zuba masa set ma kayan gado masu tsananin tsada da daukan hankali,gami da dauke hankalinka daga ainihin duniyar da kake zuwa wani ni'imtaccen guri na daban. Daga can saman yalwataccen gadon da aka qawatashi da wani tsadajjen bedsheets da comforter gami da pillows da aqalla sun kusa shida. Mutum ne kwance,wata irin birkitacciya kuma hargitstsiyar kwanciya da kana mata duba daya zakasan ba cikin nutsuwa akayita ba. Domin komai na gadon a yamutse yake,kaman yadda qafafunsa suke zube a qasa wadanda ke sanye da snickers din da ko samun daman ciresu ba'ayi ba. Idanu ta zuba masa ranta tana jin yana wani irin baci. A duniya idan akwai wani abu qwaya daya daya kasance rashin sa'arta na duniya zata iya cewa almaz ne......yana daya daga cikin miyagun qaddarorinta.......yana daya daga cikin qaddarorin data gaza sarrafasu har sai da sukaso yin wasan kura da rayuwarta. "Tasheshi" Ta fadi rai bace tana duban murdeden qaton da shine ya buda mata qofar dakin,bayan tayi dukkan qoqarinta don tayar da almaz din amma bai wani motsa ba. Hannunsa yasa ya juya almaz yana kuma wancakalar dashi gefe,har sai da mammina taji abun har zuciyarta. "Kada ka sake kwata irin wannan......kada ganinsa a haka ya sanya ka dauka wani wulaqantaccen kaya ne maras daraja......shi din daraja ce gareshi me yawan gaske". Qas yayi da kansa sannan ya furta. " A gafarceni" Kana yadan ja baya daidai sanda almaz ke buda idanunsa da qyar wadanda sukayi masa nauyi. A karo na biyu ya sake ganin inuwarta cikin idanunsa. A karo na biyu bayan hankalinsa ya fara kutsawa sassan jikinsa yana sake maimaita masa karatunta.....fuskarta......sunanta......alaqarsu......dangantarsu.......da kuma tarin wasu tsarika daya soma shiryawa kansa. Tsarikan da ya jima yana gayawa kansa ba masu cika bane......tulin mafarkaine kawai masu qaryata zahiri.....kwatsam sai wani dan mitsitsin qyalli ya wulqa da sauri ya fara haska masa wata qofa. "Ana" Ya fada da wani sauti me nauyi,wanda shi zai gaya maka zahirin nauyin dake cikin jikinsa dama hankalinsa. Idanunta ta dauke daga saman kyakkyawar fuskarsa......wannan fuskar dake tuna mata da tarin abubuwa masu yawan gaske da suka shude mata......wannan fuskar da kullum ta kalleta take tone wani birnannen abu da takejin ya kamata yayi nisan da ba zata iya koda tunawa dashi ba.......wannan fuskar dai da a haka take da wata irin kamala da nutsuwar da tasha banban da abinda ke shimfide a ruhin mamallakin fuskar. "Ku sashi ya dawo daidai nan da minti sha biyar kacal ku fito ku sameni a parlor.......babu lokaci,kafin cikar wa'adin a nemomin tamim ya iskeni a nan yanzu" Ta furta gaba daya tana juya gami da ficewa a dakin. Idanunsa ya maida ya lumshe kaman zai sake komawa baccin,saidai kuma wannan basamuden bai qyaleshi ba,ya kamashi yana tayar dashi. Bai musa ba ya miqe,don shima ya gaji da kwanciyar,yana buqatar wanda zai taimakeshi yace kwanciyar ta isa haka. Zaune kawai tayi a falon,idanunta kafe guri daya,yayin da zuciyarta ke shirya mata yadda lamarin almaz zai iya zama barazana a gareta muddin komai bai hau kan saiti ba. Mission da qudurinta akan almaz me girma ne.......wani abune da batasan yawan adadin shekaru darare da sa'o'in data laqume tana lissafin zuwansa ba. Wani irin murmushi me bayyana tsananin qololuwar nishadin da zuciya ke ciki ne ya subuce mata,saita dauke hannuwanta tana goyesu a qirjinta tana kuma ci gaba da takawa d'ai d'ai. Iya tuna yadda al'amarin zai kasance kadai walwala yake bata......wani irin sukuni yake saukar mata,tare da mantar da ita daya bangaren muhimmin aikin nata,duk kuwa da cewa wancan aikin zai iya zama mafi muhimmanci fiye da wannan.......saidai kuma ita din tana bawa MAIDA MARTANI da BADA SAKAMAKON ABINDA KA SHUKA da matuqar muhimmanci fiye da maida hankali ga abinda zai iya jawo mata asarar dukiya. Daidai lokacin suke fitowa daga dakin. Almaz yana gaba yana biye da almaz din. A karo na biyu ya sake dubanta,yana tuna shekarun daya dauka bai sake sanyata a idanunsa ba,idan ba mantawa yayi ba shekaru shida kenan cif cif. Tana nan a yadda ya santa a baya,ba wani abu daya canzata,tsufa ko wani yanayi da zai nuna shekarun mutum suna tafiya sam babu ko daya a tare da ita. Idan har yana lissafi a daidai......ganinta yana samuwa a gareshi ne bayan kowacce shekara shida,a tsahon shekarun daya dauka a rayuwarsa,shekara ashirin da tara kaman yadda yaji ana fadi,sau uku tak! Ya taba ganinta,wannan shine cikon na hudun. Gani ukunnan wani gani ne da yasha banban da dukkan wani gani da zaiwa kowanne dan adam,alaqa da kusanci da ake gaya masa wanda ke tsakaninsu har yanzu yana jinsu a wasu abubuwa da basu gama shiga damuwarsa ba......saidai a duk sanda zatazo ta tafi tana tsayewa a ransa da idanunsa da kuma tunaninsa,har xuwa sanda zata cike shekaru shidan ta sake dawowa. Dubanta yake sakeyi,yana mamakin abinda ya hanashi ganinta a shekaru shidan daya kwashe gidan prison yana zaune?......to amma kuma sai ya taqaita mamakinsa sanda ya tuna WAYE SANADIN FITARSA A YANZU DA YAKE TSAYE A NAN DIN?. (08187255862 lu'u lu'u) A nutse ta zauna tana dubansa gami da masa nuni da inda zai zauna din shima. Bai musa ba ya zauna da yanayin jikinsa da babu wani qarfi sam sam. Wani irin rashin qarfi da qwaya da kuma miyagun kayan shaye shaye suka dade da yin gaba da duk wani kuzari na jikinsa. Idanu ta sake zuba masa,kaman yadda shima ita yake kalla,saidai kafin takai ga cewa komai tamim ya shigo bakinsa da sallamar neman izini. Daga masarauta yake,kuma a wannan yammacin ya gama biyan salary din masu kula da dawakan sultane,wanda kusan duka ire iren wadannan abubuwan masu muhimmanci da suka shafi sultane a hannunsa suke. Da kayan ma'aikatan cikin gidan ya kamata ace sune a jikinsa,amma a yanzun sanye yake da wasu kaya. Wani irin yadi ne me kyau da tsada da aka yiwa dinkin 'yar shara,sai ya saka wata farar riga a ciki,sai dogon wandonta mahadin kayan,yayin da kansa ya kasance sanye da wata hula ire iren hulunan da akasan fulani na ta'ammali dasu. Shigar shigen ta fulani ce,saidai sam shi din baya zubi ko kama dasu. Abune me wahalan gaske ka iya gare yare ko qabilan tamim,don yayi kamanni da wasu yaruka na qasar niger din,kaman yadda yayi zubi sosai da su. Iya kallon mammina a gareshi kawai yana iya gaya masa matakin farinciki baqinciki ko tuhumarta a kanka. Don haka a yanzun yana shigowa ya ratsa a hankali ya yiwa kansa mazauni a inda yake ganin yafi dacewa dashi,wanda yana kammala zaman duk wani mahaluki dake numfashi a parlor din ya juya ya fice,mutum na qarshe kuma yaja musu qofar yana rufeta,sa'annan sukayi tsaye a nisan tazarar da aka lamunce musu suna kuma gadin koda tsuntsu daka iya nufar qofar da zummar shigewa. "Anya zaka iya?.....anya ka shirya aikin nan almaz?" Mammina ta fadi fuskarta a hade tana dage dukka girarta guda biyun idanunta cikin na almaz din. Duban seconds yayi mata,sannan ya janye idanunsa daga kanta yana sakin wani irin murmushi,hankalinsa kwance ya soma magana. "Ana ko?.....Duk da iqirarin dangantakar da kike a tsakaninmu.....amma har yanxu bakisan waye almaz ba......bana tunkarar komai saina shirya masa.....bana kuma tunkarar komai saina tabbatar zan iya". "Banga alama ba......" Ta fada tana katse hanzarinsa. Idanu ya zuba mata alamun neman qarin jawabi da idanunsa da suke a shanye koda yaushe saboda yawan buguwa. "Kasan a yau ya kamata nazo na sameka a shirye kana karbar horo tsarikan dana baka?!" Tayi maganan a dan tsawace rai a bace tana dubansa. Still dai baice komai ba,don a rayuwarsa ya tsani tsawa ko ka gaya masa magana kai tsaye haka kome zaka bashi. Fahimtar hakan wataqila ya sanya mammina sassauta muryarta tana dubansa. "Almaz......na baka dukkan wata masaniya,na kuma baka dukkan wani kundi......na baka shafukan rayuwarta kaf gaba daya.......tun daga quruciyarta har kawo yau.......me takeso?,me ta tsana?,me yafi burgeta?......shin me ya rage maka almaz?.....me ya rage banda nazo na sameka ka fara qoqarin zama irin wannan mutumin?.......ko kasan daga yau ya kamata komai ya fara motsawa?,daga yau ya kamata ace komai ya fara tafiya?". Shanyayyun idanunsa ya janye daga kanta,tsaki yakeso yaja saboda hayaniyar da take masa amma ya taushi kansa. "Wannan yarinyar.......tsaurinta da tsarinta yayi yawa,banga kuma ta inda zan farauto soyayyarta harta aure ni ba". "Dama kana tunanin kyanka iya kalamanka ko wani quality dana tabbatar baka dako daya ne zaisa ta soka ta aureka?.......a matsayinka na qasqantacce maras daraja?!.....ni zaituna ni zan sanya akhnan ta aureka ba tare data shirya hakan ba......ni zan tsara yadda zata mallaka maka zuciyarta bawai qoqarinka nakeso kayi wajen faruwar hakan ba......kawai kayi qoqarin daidaita kamalarka da hankalinka......kayi qoqarin zama BASARAKE kayi wanka da ruwan da 'ya'yan sarakuna keyi......ka siffantu da IZZA wadda ita daya ce makamin daka iya janye hankalin biftu akan d'a namiji. Izza gadonta ce......izza wani abu ne a jininta,so dole taso namiji ME IZZA ba tare da tasan da wannan abun cikin ranta ba" Takai qarshen tana nuna qirjinta. IZZA da mammina ke maimaitawa ta sanya yaji ya kwadaitu dason ganinta. Shima a jininsa ne......mace me izza tana burgeshi.....ba mace ba koda namiji ne me izza hakan yana qawatar dashi,to amma dole ne kaman yadda ta buqata ya saisaita nutsuwarsa. Zata iya hangen finsa samun alfanun komai......to amma kuma shi yana hangen alfanun da zai samu saiya ninka nata. "Dole kayi nisa da dukkan wani nau'in kayan maye......dole ka haqura dasu na wasu watanni......kana iya ci gaba bayan komai ya saitu ya kammala......amma yanzu kyanka da hankalinka mukafi buqata" Ta fadi da sautin dake nuna da gaske kowacce kalma ke fita a bakinta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 67 ____________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Idanunta ta juyar zuwa ga tamim tana maida kallonta a kansa. Bai zaci zata maida dubanta a kansa haka da wuri ba,sai yayi saurin sake sadda kansa qasa saboda nuna tsantsar biyayya.....saidai kuma,can qasan ransa da zuciyarsa wata iri nau'in wuta ce me zafi take tartsatsi. "Nutsuwarsa tana hannunka........a duk lokacin daya sake fita daga saitinsa laifin baya wuyan kowa saikai.......zansan yadda za'a rage maka ayyuka da nauye nauye a masarauta......don ka samu cikakken lokacin tarbiyyantar dashi da al'adu da yanayin sarauta ta yadda zatabi jininsa........abu na qarshe daga yau.......daga kuma sanda zai fara fita don sajewa da mutane da shiga masarauta,sunansa ya sauya daga almaz......sunansa ya koma FARRE ABBA JALAAL sunansa dana mahaifi". Jinjina kai tamim yayi da wani irin nauyin dake gwada ya karbi dukkanin umarninta,ta miqe a hankali tana takawa. "Zan aiko da yalwa da wasu CFA din da dukkan adadin nauyin da kuke buqata....." "Godiya nake uwar gijiyata" Ya fadi yana tattara dukka qarfin halinsa ya miqe,daidai sanda almaz ya karkace ya koma saman lalallausar sofa din yayi kwanciyarsa yana ji a ransa duk duniya bai taba jin abu me laushi kaman gadonsa na can dakin ba da kuma wannan kujerar. *AKHNAN* Da qyar takai kanta daya daga cikin bedrooms dinta,ta kuma samu ta zube saman gadon da yake shimfide da wata shimfidar alfarma tana tura kanta cikin comforter din dake saman gadon tana jiran a buqaci amfani da ita. Batasan yaya ba......bata kuma san daga ina ba,dukkan wani qwarin gwiwarta ya soma kwaranyewa. Dukkan wata jarumta tata ta soma sulalewa tana barinta da iya zallar halinta,abinda ya sanya wani irin kuka tsinke mata,a karo na farko tun bayan data mallaki hankalin kanta da kuka me nauyi irin wannna me cike da kadaici ya tsinke mata. Wani irin kadaici kawai takeji yana ratsata,tana maimaita kiran sunan mammina. Ina mammina ta tafi ta barta a irin wannan yanayin?,a irin wannan lokacin da tafi buqatarta sama da ko yaushe?,a irin wannan lokacin da komai yake shirin jagule mata?. Ko da imagination ba zata ita hakaito hakeem a mazaunin mijinta ba......koda zata rasa soyayyar sultane ba zata iya aminta da hakeem a mazaunin mijinta ba. Hakeem fa?,mutumin da yafi dukkan mazan da suka taba zuwa don ganawa da ita qansqanci?,mutumin da shine mafi qaranci matsayi......daukaka.....wayewa da sanin ilimin zamani dame duniya take ciki?. Ba hakeem ba......koda wanda ya fishi komai.....koda wanda zai iya cika sharudda ya kuma hada qualities din da takeso bata jin zai samu amsa cikakken sunan miji a gareta,ballantana hakeem din da ko cikin 'yan uwanta na jini ba zata lamunce masa ya samu ba. Malamin addini fa?,me qarancin wayewa?,banda bai iya boko ba sam.....wanda baisan komai ba sai karantarwa......baisan komai ba sai wa'azi?,bazai taba iya tsaiwa a guraren data tsaya ba a duniya,cikin dubban yaruka.....cikin dubban masu jajayen kunne......cikin qwarrarrun doctors masana masu tsananin wayewa. Tana running company irin sahel couture taje ina da malamin addini?,tana zuwa taruka na duniya da qasashen da suka isa,ta tsaya gabansu tayi magana da salon harshen da yake burge kowa ya kuma girgiza kowa,ya daga darajarta......ina zataje da malamin addinin da baisan kowacce kalar wayewa ba?. Me yasa sultane bazai fahimta ba?,me yasa bazai gane babu kima ko guda daya game da wannan tunanin nasa ba?. Hankali kwance take takowa cikin gidan,a nutse kuma tana karantar akwai wani abu daya canza tattare da gidan. Motsi da karsashin da kowa keyi yadan ja baya kadan,abinda ya alamta mata akwai abinda ya faru tabbas da gaske kuma. Sanda qafafunta suka taka sassanta yalwa ta hange tsaye tana jiran isowarta,wanda ganin shigowarta ya sanya yalwa matsowa cikin girmamawa. "Allah shi baki yawan rai......ina tunanin akwai matsala yau cikin gidan nan,akwai damuwa" Yalwa tayi maganan da sautin da zai sanya ka tsammaci batasan komai ba,bata da masaniyar komai daya faru. "Me ya faru?" Mammina ta fadi tana zame takalmanta,daya daga cikin hadimanta ta tsugunna tana kwashesu gami da ajiye mata wasu masu sauqi ta soma zura qafafunta a ciki. "Gimbiya akhnan ce.....ta shigo dazu a birkice tana nemanki,kiran sunanki kawai takeyi". Sosai fuska da yanayin mammina ya sauya yana juyawa zuwa yanayi na razana. "Me ya faru da ita?,me ya sameta?,me yasa ba wanda ya sanarmin?,wanne irin sakaci ne wannan da rashin sanin martaba da muhimmancinta?,hakan yana nuna kenan ko bayan babu raina babu wanda zai iya kula da ita?,ba wanda zai iya kula da damuwarta?,ina morsa safiyya?,me yasa batayi komai akai ba?" Tayi maganganun cikin fadan daya sanya kowa ya sake rissinar da kansa,suna jin tabbas su masu laifi ne,jikinsu kuma yana sake yin sanyi. Dukkaninsu sunsan cewa akhnan din wata halitta ce me matuqar muhimmanci a garesu......ita din wata halitta ce da damuwarta taba ta ko shiga rayuwarta kayi mata wani abu na ba daidai ba babban kuskure ne a tare da kai. "Muje na ganta" Mammina ta fadi tana sauya akalar tafiyarta zuwa kebantacciyar hanyar da zata sadata da sassan akhnan. Daga yanda taga dukka hadimanta a cure a guri daya ta tabbatar lallai abun babbane,hankalinta ya tashi hankalin kowa ma a gidan ta tabbatar sai ya tashi. Da alama ta shiga wannan yanayin nata na tsananin fushi da fusata,tasan kowa dole yaji a jikinsa,komai nata kuma zai canza. Tako ina gaisuwa suke saukewa mammina din,suna kuma sake rusunawa zuwa qasa. "Me kukeyi a nan?,meye amfaninku da kuka barta ita daya a ciki kuka dawo nan?!" Ta jefa musu tambayar a tsawace tana dubansu. "Allah ya huci zuciyar giwa.......ita ta buqaci hakan,dole ne cika umarnin gimbiya akhnan,mun nisanceta ne bawai don haka yake muradinmu ba" Birra ta fadi cikin tsantsar ladabi. Shuru tayi dake nuna alamun tana calming fushinta,sannan ta juya a hankali tana wucewa qofar farko da zata fara sadaka da sitting room da falukan alfarma kafin kakai ga isa ainihin shiyyar bedrooms dinta. Dan qaramin murmushi ta sauke,duka falukan ba gilmawar kowa sai na'urori daketa aiki abinsu suna bada qara mara sauti sosai wadda bata da damuwa sam. Ta dora hannunta kan qofar dakin data gani a bankade ko.maidata ta rufe bata samu daman yi ba,ta tura da sallama,sannna ta lalubi makunnin hasken dakin ta kunna,take haske ya gauraye dakin,daidai kuma sanda ta miqe daga saman gadon sukayi ido hudu da mammina din. Da sauri ta ture comforter din kuka yana sake narke mata,ta sauko da sassarfa ta nufo mammina tana jin duk duniya damuwarta ta yaye da ganin mammina kadai da tayi. "Meye haka biftu?......me ya sameki?,waye ya sakaki kuka?" Dukka mammina ta hada tambayoyin ta jefa mata su tana ware hannayenta akhnan din ta shige ciki tana sakin wani kukan. "Sultane ne mammina......sultane ne" Ta qarasa maganan da yanyin da zai gaya maka zallar sakalci da gata data samu a dukkanin rayuwarta. "Subhanallah......sultane dai kuma?,me kikayi masa?" Ta tambaya tana dan bubbuga bayanta alamun lallashi. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Don na sallami hakeem......bana sonshi mammina baiyimin ba,malamin addini ne fa mara wayewa sam sam.....yanxu kina ganin irin wannan mijin ya dace da d'iyarki?" Ta fada tana jin cewa matsalarta tazo qarshe. Ko kowa bai fahimceta ba mammina tana fahimtarta,ko kowa bai kawo mata mafita cikin matsalolinta ba mammina tana kawo mata,ko kowa bai goyi bayanta ba mammina tana goya,tsanani.....wahala ko dadi basa sanyawa mammina ta janye mata ko ta daina goyuwa da bayanta. Wannan karon ga mamakinta sai taji mammina na zameta daga jikinta,abinda ya tilasta mata daga kanta a hankali tana duban mammina din cikin zallar mamaki. Mamakin ya sake ninkuwa yadda taga mammina na dubanta da wani irin kallo,wannan tausayin.....wannan tausasawar.....wannan laushin dukka babu su. A hankali mammina ta soma girgiza mata kai. "Wannan karon.....idan har kin bijirewa maganan sultane,idan har kin kasa biyayya wa umarnin sultane,to tabbas bana tare dake......". Mamaki ya tsayar da kukan akhnan gami da wani dan siririn firgici daya ratsata. "Mammina......ke kikamin alqawari fa". Kai ta daga a hankali tana takawa da baya. "Nice akhnan......saidai akwai abubuwa da dama da suka tilastamin tunanin janye wannan alqawarin........morsa safiyya,nice mutum ta farko da zata kalla wadda ta zigaki ta kuma doraki akan turbar bijirewa maganan sultane....." "Morsa safiyya!......morsa safiyya!......har yau har yanzun dai ita!......ita kadai ce matsalata a dukka wani cikar muradina?,itace damuwata a dukka burikana?!......qanwar uwata ce amma BA UWATA BACE!......ba itace ta haifeni ba,kin yarda mammina WATA MACE CAN ta shiga tsakaninki da tausayin dake zuciyarki game da 'yarki?" Ta fadi da wani irin zafi bacin rai da kuma tarin gungun tsanar morsa safiyya sabo daya bude shafinsa cikin kwanyarta. Wani abu ne me girma ya motsa can qasan zuciyar mammina. Ta samu nasarar dasa DASHE na farko,wani sabon babin sabon aikin da zai zame mata sharar fage a dukkan komai da zai biyo baya. "Akhnan......ko kinaso ko bakiso morsa safiyya wani bangarene me girma na rayuwarki.......tana da matuqar muhimmanci a rayuwarki......ita din jininki ce........wata sashe ce ta rayuwarki,jini iri daya ne yake yawo a jikinku......ko baya ga wannan SULTANE zai iya shiga sahun mutanen dake zargin akwai sanya hannuna kan dukkan wani abu da kikeyi,akwai sa hannuna akan duk wani abu da kike aiwatarwa.......musamman idan hasashe na ya tabbata yi masa tunani akeyi.......ba shine yake tunanin ba,bazanso bata wannan alaqar ba......bazanso rasa wannan yardar da amincin da yayimin akanki ba,akan zan iya kula dake.....akan zan baki kalar rayuwar da MAHAIFIYA zata bawa 'YARTA,wannan karon dole ki biyayyawa umarnin sultane" Tana kaiwa fuskarta na nuna wani irin narkakken qauna da tausayin akhnan saman fuskarta. Sai ta juya tana ficewa a dakin. Sulalewa tayi kawai ta zauna gefan sofa,tana jin komai tana kuma ganin komai kamar wata almara,kamar komai ba gaske bane. Yau ita mammina ta kwarewa baya?. To amma still idanuwanta suna iya hangen raunin mammina cikin dukka maganganunta,idanunta suna iya hangen wani abu me kama da qauna da kuma tausayinta cikin ranta......wannan kawai ya isa ya tabbatar mata da gaske mammina zata tilastata ne kawai tabi sultane saboda tsoron hukuncinsa......zata tilastata ne tabi sultane saboda gudun xamowarsu masu laifuka dukkaninsu a gurinsa. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 68 ___________________________ Bononza bononza https://wa.link/l1gcz8 Assalamu alaikum yan uwa mata masu albarka Zuzeam ventures zatayi promo karshen wannan watan har zuwa cikin watan nan me kamawa insha allah -Da 6k kachal zaa baki kaza da ciccibi da gari da tsumi da gumba pills shaki matse masu kyau da ingancin dazai sakaki dawowa ki qara harma ki kawo wani, -Da 11k zaa baki kaza full da ciccibi da gari da tsumi da gumba, da maganin sanyi wannan promo ne akan murnar cika shekara 10 cif da fara sanaa a online Dan haka duk wadda take bukatar shiga cikin wannan promo Dan samun wannan garabasa to tayi sauri kafin ta kare Kuma ku sani tsakani da Allah zaayi wannan promo komi me inganci ne Kyau sosai zaa baku tsakani da Allah Idan kinada 4k ma zaa baki ciccibi kawai sai gari da tsumi masu kyau da ingancin suma, Dan haka duk wadda take da bukata kofa a bude take Idan kinada Yan uwa da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka Karku manta promo kwana 3 ne an kare insha Allah ___________________________ "Bazan iya ba wallahi......bazan iya auren hakeem ba......ban shirya rayuwa qarqashin ikon kowa ba,gashin kaina zanci gaba daci.....halastaccen 'yanci da babu takurawa ko kuma qunci a ciki" Ta fada tana girgiza kanta.. ★★★Kwanaki biyun da suka biyo baya sun zamo wasu irin kwanaki ne da suka sauya launi da kalar rayuwar wasu cikin gidan. A kwanakin komai na gidan yana nuna akwai wani kwantaccen abu dake faruwa cikin gidan,kwanaki ne dake sake bawa ko tabbacin da gaske akhnan itace zuciya kuma hasken gidan. Sai komai ya zama wani iri,kowa cikin takatsantsan da walwalarsa yakeyi kada taci karo da yanayin da ake ciki a wannan lokacin. Kwana biyunnan cur ba wanda ta bari ya ganta,kaman yadda bata bari taga kowa ba,koda aisa shehnaz ma. Koda sultane baiyi wani yunqurin nemanta ko neman sake ji daga gareta ba,ya riga ya gama yanke hukuncinsa a wannan karon,ya kuma tsayarwa da ransa ba abinda zai sanyashi janyewa. Baya son ya bata kowacce irin dama da zata sakata jin cewa akwai yuwuwar ya janye nufinsa ko ra'ayinsa,don haka hatta da mammina ko morsa safiyya baima zauna yayi zancan da kowa ba,shirinsa kawai ya farayi na yadda komai zai kasance. Nannie kawai ya saurara har suka tattauna ta nemi ganinsa akan batun,ranta a matuqar bace,hankalinta kuma dukka a dagule,cikin tsananin bacin rai tana fadin. "A wannan karon ka barni,sai naci mutuncin biftu......wai shinma dame aka halicceta ne?,da qarfen lu'u lu'u ko na gold da zata dinga wulaqanta mutane masu daraja?,masu darajanma irin hakeem......malamai magada annabawa?,masanin ilimin da zai kaika tudun muntsira?.....fatan kuma kowanne musulmin kirki kenan?" Ta qarasa maganan a sanyaye. Murmushi kadan sultane ya saki,irin murmushin dake cike da nutsuwa da sanin ciwon kai. "Duk maganan nan da kikeyi fatima bata baki ne.......karki cewa khadeejatu komai,kulawa ma ai yabawa ce,tayi duk abinda zatayi,ban gani ba,bansan kuma abinda zai saukeni daga wannan hukuncin dana yanke ba". Kai Nannie ta jinjina,hakan daya fada da kuma tsaiwarsa akan hukuncinsa wannan karon ya mata dadi,amma can qasan ranta tana jin wani dan rashin dadi kadan,kaman hakan zai zama takura da auren dole ga akhnan din kenan?,bayan Shehnaz da aisa kowaccensu an bata dama ta fidda wanda takeso?. "Amma yaaya.......tun jiya aisa tacemin tana sassanta,taqi yarda ta fito taqi kuma yarda taga kowa". "Shirme kenan,tayita zama,idan ta gama zata gaji ya fito" Ya fada cikin rashin bawa maganar wani cikakken muhimmanci. "Yaaya" Nannie ta sake fada. A nutse sultane ya aza dubanshi a kanta,da alama dukkan wannan qwarin ran da fadan da takeyi akan akhnan raunin nan irin na diya mace yana tattare da ita. "Ina saurarenki" Sultane ya fada yana tattarawa Nannie hankalinsa. "Nace anya ba jinnu ba sihiri a al'amarin biftu?" Tayi maganar qwayar idanunta suna nuna da dukka gaskiyarta take maganan. Shuru ya ratsa a tsakani na wasu sakanni,kafin daga bisani sultane ya saki wani murmushi. "To......gida dai irin namu ba za'a ce bamu da mutanen boye na gado ba,mutanen boye na ainihin kan gidan ba,amma ba masu cutarwa ba,ba wandada zasu dinge bige mana d'iyoyi suna faduwa ba suna sakasu fagamniya ba......sihiri kuwa ba wani a waje daya isa ya jefi daya daga cikin zuri'armu ya kamashi.......saina cikin gidan,a cikinmu kuwa bana zaton akwai wanda zaiwa biftu wani mummunan aiki.....ko akwai?" Sultane ya qarashe tambayar yana duban nannie. Kai ta girgiza a hankali,dukka maganganunsa tasan haka suke,ko ita kanta shaida ne,ta taba rayuwa da kishiyar da tace nata aikin asiri da jifa ne,qarshe ya koma mata da wani irin zazzafan haukan data dinga yinsa har ya zame mata ajali. Tabbas ga dan waje cinsu da asiri bame yuwuwa bane,cikin gida kuwa tsakanin ahalin sultane,takun saqa da sabani irin na harshe da haqori dole akwaishi......amma bata tunanin asiri a ciki. To shin ma idan akace da asirin waye zaiwa biftu?. Morsa safiyya duk duniya bayan sultane tafi kowa kusanci na jini da akhnan.....ba yadda za'ayi uwa ta jefi diyarta da asiri. Mammina kuwa......wani abu ne da sam hankali bazai dauka ba......sam tunani da sharrin me sharri ma bazai biyo ta gurin ba. Matar data zame mata uwa tun tana da shekaru hudu a duniya?......ta zame mata wata irin garkuwa abar misali. Tabata zaifi zuwanma mutum da sauqi akan taba akhnan. Dukka tunaninta da damuwarta kan yadda akhnan zata rayu cikin 'yanci da walwala ne,to waye zai aikata wani mugun abu a kanta cikin mutum biyun???. Qatuwar tambayar data sanya ta bawa kanta amsar yin tambayar ma ba abu bane me ma'ana. "Ki rabu da ita kawai,zatayi dukka ta gama,munyi aure da safiyya kuma mun zauna shigen wannan zaman,amma yanxun bai zama tarihi ba?" Ya fadi yana duban nannie. Murmushi ya subucewa nannie din harma sultane din yana tayata. Ta sani shima ya sani,kowannensu ya tuna wani abu ne daya shude da zamewarsa tarihi ya zame musu wani abun tunawa da sanya dariya. *KWANA NA UKU* Yammaci ne dake dauke da wani irin lullumi da ya bada wani sassanyan hadari daya wanzar da canzawar launin sarararin samiya zuwa ruwan toka toka. A dukka sasannin qasashe da suka samu irin wannan yanayin daya kasance tamkar wani sassauci ko rahama daga ubangiji na zafin daya dinga koda mutane a kwana biyun da suka shude,irin zafin damina dake tayar da hankali ga duk mutumin da bayason zafi. Daidai lokacin da mammina ke zaune farfajiyarta ta musamman,tana kuma ganawa da baqin data zabi iya wadanda take buqatar ganawar dasu. Su uku ne a yanzun a gurin,Shehnaz aisa mammina din sai kuma yalwa data kasancd mutum ta hudun. Dukkaninsu saman qawatattun kujerun gurin suke,hakanan akwai yawaitar kayan marmari dana maqulashe aka zube a gurin da duk me buqata ya dauka yayi amfani dasu. "Ina jinku 'yammatan sultane" Mammina data ajiye wayar data gama amsawa ta fada cikin mayalwacin murmushi gami da nuna tsantsar kulawa a kansu. Aisa ce ta ajiye wayarta a gefe,sannan ta jawo wani file ta tura gaban mammina. "Mammina.......game da sabbin muqamai da ma'aikatan da aka dora ne a sahel couture......munso muyi maganan da biftu amma har yanzu hankalinta bai jikinta,ba wanda yake samun damar ganinta ma". Ido ta zubawa file din kafin ta dubi aisa cikin mamaki. "Wani abunne yake faruwa a sahel din?". Tayi tambayar da yanayin dake nuna zallar kulawa. (08187255862 lu'u lu'u paying) "A zahiri ba wani damuwa bace ta fili" Shehnaz ta fadi kai tsaye. "To me ya kawo qorafin 'yammata?" Mammina ta fadi tana sanya yalwa bude mata file din tana bibiyar rubutun ciki. Dukkaninsu duban mamminan suke suna jiran ta kammala,cikin qasa da mintuna ta gama,yalwa ta maida ta rufe. "Ban gano wani damuwa ba a ciki 'yammata" Ta sake fadi da wannan shimfidadden murmushin kan fuskarta. "Akwai abubuwa da yawa muke buqatar qarin haske mammina.....nidai bazanyi qarya ba,ta bangaren office dina kusan komai a makance yake tafiya,ba komai na fiya fahimta ba,akwai muqaman da aka bayar kuma da suna buqatar dogon nazari kafin a bawa wadanda aka bawa din,ko kuma a jira dawowar CEO ta rattaba hannun amincewa da hannunta". Shigar mammina maganar tayi da wani sauti da tajishi ba'a daidai ba,amma saita tsaurara kallonta akan fuskar aisa din tana sake fadada fara'arta. "Ina kyautata zaton baku samu kunyi kowacce magana da akhnan din ba?......banda abun aisa,ai ba akhnan ba,ko ke ina da ikon zartarwa ina da ta cewa a rayuwarki ballantana akhnan......" Yadda tayi maganan sai aisa taji kaman tayi maganana muhallin da bai dace tayi maganan ba,kaman tayi rashin kyautawa a ciki,kamar kuma mammina taso fahimtarta baibai. "Ayimin afuwa......tambayata bawai tana nufin wani abu na daban bane,inaso ki fahimceni da kyau,da akhnan da sahel couture dukkaninsu amanarki ne dana sultane a hannunmu,bazan manta wannan maganan naki ba,gata nan na baku amanarta.....ku kulamin da ita kowanne qarshen sati idan baki gayawa shehnaz hakan ba ni zaki gayamin,amana ba abar wasa bace......sahel couture shine zuciyar dukiyar akhnan,zuciyar dukiyar masarautar agadez,dukkaninmu mun aminta zamuyi aiki cikinsa ne bawai don bamu da tamu dukiyar ba......muna aiki cikinsa ne don kawai sadaukarwar da zamu iya yiwa kowa a cikinmu idan buqatar hakan ya taso.....yin wasarere da irin wadannan abubuwan zai iya zama cin amana ne,zai kuma iya haifar da matsalar da bamusan qarshenta ba a gaba". "Well done" Mammina ta fada cikin salon burgewa tana dan tafa hannuwanta. "Ashe muna da talented girl har haka ban sani ba......ma sha Allah aisa" Mammina ta fadi tana sauke qafafunta qasa cike da tsananin nuna jin dadin dukkan bayanan aisa din. "Na sake samun nutsuwa,na kuma sake samun tabbacin akhnan tana tare da sisters din da babu irinsu.......yanzu gayamin kanki tsaye me kike buqatar ayi?". Ta fada tana miqawa aisa takarda da abun rubutu. Kadan aisa taji zuciyarta ta saki daga tarin saqe saqen da takeyi,tadan rusunawa mammina din "Basai na fadi ba,kaman zaki fimu sanin abinda ya dace mammina". Kai mammina ta girgiza. " Yadda kika gano dukka wadannan abunuwan na tabbatar idan nabar kwanyarki tayi aiki yadda ya dace za'a samu result me kyau". Kai aisa ta jinjina,tabbas daga farkon wancan watan zuwa yanxu tana ganin abubuwa da yawa a kamfanin da bata gane musu ba,take kuma ganinsu kamar ba'a daidai suke ba,tunda har mammina din ta bata cikakkiyar damar yin magana zatayi maganan. "Ina ganin a dakatar da daukan ma'aikata da kuma rarraba muqamai da ake tayi a yanzu,ayi limiting fitar kudi da siyo wasu kayayyaki da kamfani ke da buqata.....wadanda aka Riga aka dauka kuma yana da kyau a auna amanarsu da ingancinsu kafin a sakar musu komai......saina qarshe,ina ganin a rufe office din biftu......a barshi a rufe,a dakatar da dukka ayyukan da suka shafi office din har sai bayan ta dawo". "Ke zaki karbi office din ciki gaba da gudanar dashi" Mammina ta fadi kai tsaye hankali kwance cikin confidence idanunta cikin na aisa. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 69 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Dubanta itama aisa din takeyi,haka kawai cikin kanta takejin wani abu daban yana amsa kuwwa da maganar mammina. Wani abu ne da bata taba tunani ba,wani abu ne da bata taba kawoshi kanta ba,kuma wani abu ne da ita din bata taba sha'awarsa ba. Jagorancin office din akhnan wani abu ne daban da tayi imani ba kowanne mutum bane zai iyashi. Dari bisa dari dukkaninsu sun aminta da akhnan din ta musamman ce,tana da wani irin fikira da hazaqar tsara abubuwa da sanyasu a guraben da suka dace,lissafinta daban yake kaman yadda kwanyarta take daban......baya ga haka ma kuma tana ganin babu tsaro sam sam gurin bude office din CEO guda aci gaba kuma da tafi dashi,tana ganin akwai hatsari cikin hakan,ba kuma tsari akai. Wadannan lissafin ya sanya aisa din sakin murmushi,ta kuma girgiza kai. "Mammina......tu n'as aucune à quel point ta fille est incroyable(bakisan wacce irin d'iya gareki me ban mamaki ba).....ba wanda zai iya tafi da l'enterprise sai akhnan din". Yanayin fuskar mammina ne ya sauya,tadan tsuke fuska tana duban aisa. "Aisa?.....yanzun ace akhnan babu ita,ko dalili ya sanya ba zata iya ci gaba da gudanar da aikin ba,shikenan komai ya tsaya?." Kai aisa ta girgiza a hankali. "Hakan bazai faru ba......" "Daga yau na hukunta kece a mazaunin CEO.....ina fatan zaki riqe amana da jajircewa har akai lokacin da 'yar uwarku zata dawo daidai". Tayi magana tana yin rubutu saman wata takarda,sannan ta turata gaban aisa,da alama tana buqatar sanya hannunta. Kai aisa ta daga tana duban shehnaz,itama shehnaz din ita take kalla,sai tayi mata sign da idanu na ta karba din,amma sai aisan ta zare dubanta daga kan shehnaz,ta maida kan mammina tana dan sakin murmushi. "Zanje da takardan tukunna kafin saka hannu,idan na saka din zan dawo miki da ita". Kai ta gyada a nutse. "Baki da damuwa,Allah yayi muku albarka ya qara hada kanku" Ta fadi tana nuna tsananin kulawa da taushinta. Da idanu take bin bayansu da kallo sanda suke ficewa suna barin gurin,har sai da suka kammala ficewa sannan ta dauke dubanta tana sakin wani murmushi. Gyaran murya yalwa tayi wadda ke zaune a gefanta,abinda yaja hankalin mammina kenan ta maida dubanta ga yalwa,sai yalwa din ta sakar mata murmushi. "Akwai wani sabon karatun hala uwar dakina?". Jinjina kai sosai mammina tayi tana dauke idonta daga kan yalwa. "Wani lokaci kina da son jin gulma yalwa" Dariya yalwa ta saki tana sake yin qasa da kanta. "Ba son gulma bane Allah ya baki dogon kwana....kawai dai na sani,a dukkanin motsinki.......a dukka wani abu da zaki aiwatar.....dukkan wani second qwaya tak na rayuwarki darasi ne ga duk wanda ya rabeki......tabbas a wannan motsin akwai wata maganar......akwai wata hikimar,akwai kuma sabon aiki....sabuwar kwangilar da na tabbatar ta sake shigowa da sabbin jerin sahun sunayen da babu su asali a cikin aikin" Murmushi sosai da yafi kama da dariya mammina tayi tana dunqule hannunta guri guda kaman wadda ta kama wani abu. "Daya daga cikin abinda ya sanya na zabeki kenan,daya daga cikin abinda ya ya sanya nake kuma sonki kenan yalwa......kina da saurin kama abu da zaquloshi" Ta furta tana miqewa tsaye. "Tabbas......wasu sun shigo tsarin......wasu kuma sunayensu sun fice.....akwai yuwuwar shigar wasu kuma a nan gaba,don suna tsakanin gaba ne......saidai ki sani yalwa,ita matsala daga sanda ta qunshi ciki kake rainonta.....kake kula da ita......daga sanda ka fahimci tana yunqurin haife wannan abinda yake cikin nata,hakan yana alamta maka sabbin rassa take shirin zubawa.......sai kayi dukkan me yuwuwa wajen murqushe wannan naqudar......" Saita waiwaya tana duban yalwa "Idanma fa har kayi saken da matsalar taka ta qunso wani abu kenan" Ta qarashe maganar da wani yanayi a idanunta da kuma muryarta. Kai yalwa ta jijjiga alamun fahimta ganewa da kuma gamsuwa. Tana kuma sake juya girman iya tsari iya yaku da iya tafi da komai cikin wani madaukakiyar basaja da bad da kamanni. ★★Magazine na qarshe ya rufe ya kuma dorata a hankali saman sauran magazines din da suke gefansa yana furzar da siririyar iska daga tsakiyar tausasan labbansa dake da wani irin launi da yanayi me jan hankali. Tun sanda yazo agadez ya zame masa dabi'an duba jaridunsu. Da farko me kawowar ya tsaya mamakin me zaiyi da jaridu?,bayan a iya abinda ya sani bai iya yaren French ba ballantana ya fahimci abinda suke rubuta ba,saidai abdii ya datse wannan mamakin ta hanyar fadi masa. "Abinda akace kayi kenan". Cikin ran abdii yana masa kyakkyawan uzuri. Ko shi yasha mamakin yadda captain obbo ke iya sarrafa yaren English da French a harshensa,kai kace yana yara yaren oromo ne,hankali kwance da wani irin qwarewa da accent din da ko cikin mafarki zai qaryata cewa captain obbo dinne. A hankali yake karantar cewa aikinsa ya dace dashi,hakanan aikinsa ya dace da yanayinsa.....komai nasa yana da wani irin sirri,yana kuma da wani irin tsaro. Ba komai daya shafeshi yake bari a sani ba,sai abinda shi din ya aminta ko ya yarje maka ka gani ko kuma ka sani. Sau da dama dabi'unsa na bala'in burge abdii din,harma yakan zauna ya dinga imagination na kanshi a matsayin muhammad haisam din. A nutse ya miqa dogon hannunsa ya jawo wani dan littafi dake dauke da calendar din shekarar da muke ciki gaba daya. Watanni goma sha biyu ne a ciki,ba kaman calendar qasarsu Ethiopia ba,da su suke da watanni goma sha uku a shekara. Duba kwanan watan yau yayi,wanda a kansa yayi cycling dinsa da maka,wannan ya tuna masa schedule dinsa na yau,sai ya maida calendar ya ajiye,ya zaro wayarsa ya soma kiran hussam. Bugu daya ya dauka,cikin girmamawa da barkwancin nan nasa ya soma gaidashi. "Barka da rana captain obbo". Numfashi yaja kadan yana lumshe idanunsa,ya rasa me yasa duk yadda yakai ga tsare gidansa sai hussam yayi wasa dashi?. Nanay kanyi dariya,duk da kasancewarta bame yawan magana ba,takance. "Yana kallonka a matsayin sakonsa,ya manta cewa inda Allah ya qaddara amud yana raye shine sakonka". Zuwa yanzun ya soma sabawa da halin hussam,ba komai bane yake bashi muhimmanci ba......a haka yaci nasarar soma sauya masa halaye na maida abubuwa serious daga kasu ashirin zuwa kaso tamanin. "Barka......ina fatan kowa yana lafiya?". "Alhamdulillah......se kewarka da kowa keyi,nanay nata boyewa.....amma ni nasan hakan koda zata boye din kuwa" Boyayyen numfashi haisam ya sauke,ya sani nanay zatayi kewarsa akan kowa,daga ita kuma sai noorah daya tabbatar ita zata biyo bayan nanay din. Akwai shaquwa da qauna sosai tsakaninsa da 'yan uwansa.....hakanan ko a tsakanin junansu akwai wata soyayya me yawan gaske. "Nan kusa in sha Allah.......yau nawa ga wata?" Haisam ya dora kai tsaye akan dalilin kiran. "Sha takwas obbo" Kai ya jinjina a nutse. "Dukka security din bangaren motii,dana bangaren nanay zasu bar bakin aiki a yau.......inaso su koma bakin babbar qofa,na babbar qofa dana kewayen gidan gaba daya aikinsu zai dakata.....za'a kawo wasu yau,bana buqatar ka sanar da kowa,zanyi magana daga headquarter,zasu zo su kwashesu su kuma kawo wasu" Yayi magana da calmness dinnan nasa dake nuna adadin rashin son hayaniyarsa. Shuru hussam yayi,yanason tuna watannin da kwata kwata mutanen sukayi. Wannan wanne irin aiki ne da yake sanya obbo din rashin yarda da kowa,musamman akan motii da nanay?,idan zai iya tunawa cikin shekara biyu kacal an canza masu tsaron wadannan gurare sau uku kenan. Yana ji a jikinsa akwai wani dalili daya sanya yake irin hakan. Wani irin tsaro yake bayarwa a dukka wani gilmawa tsakanin sassan motii dana nanay dama fadarsa da muhalli da guraben zamansu. Irin wannan abun ya sanya masarautar jimma ta zama ta daya,kuma ta daban da sauran kowacce masarauta dake cikin Ethiopia,masarauta mafi girman izza da fadin mulki,tsananin tsaro da wani irin tsari daya sanya idanu da yawa suke kanta. "Amma obbo......." "Karka tambaya.....umarni nake baka,ba labari bane ko shawara". (08187255862 lu'u lu'u paying) " An gama" Ya fadi cikin girmamawar nan dake a tsakaninsu tun asali. Sai haisam ya zare wayar daya kunnensa kawai ya kasheta,sannan ya dorata a hankali saman table din dake kusa dashi. Lallausan farin tafin hannunsa ya miqa me dauke da zara zata yatsu yana kalla. Wani irin abu yaji ya tsarga masa tun daga cikin tafin hannun nasa zuwa sassan jikinsa,wanda sai daya tilasta masa lumshe idonsa kana ya budesu yana jin wani abu na bin jikinsa. "Astgafirullah" Ya maimaita har sau biyu. Besan me yasa abun yaqi bacewa daga jikinsa dama idanunsa ba,tun daga ranar shudewar awannin da kwanakin basu sauya komai ba. A duk bayan wucewar wasu lokuta sai yaji komai ya dawo masa kaman a sannan hakan ta faru. Tafin hannunsa tsakiyar nata tafin hannun me wani irin dumi da laushi. Hannun nasa ya maida ya dunqule yana mutstsukashi a hankali wai ko zai daina jin abinda yakeji din,ranshi na baci a hankali,siririn tsaki yana kubce masa. Itace mace ta farko da hakan ya fara faruwa a tsakaninsu. A hankali tunaninsa ya koma baya,yana tuna wancan ranar a hippodrome,kalamanta cikin gidansu na ranar juma'a dana washegari asabar. Wani tsakin yasake fusga daga harshensa yana jin wani bacin ran yana sake d'iga saman zuciyarsa. Yana jin nauyin zunubin data jawo masa ya dauka,girman zunubin taba jikin macen da ba taka ba,wadda annabi muhammad S A W yace ya fiwa mumini sauqi ya zauna a samu qusa a kafa a saman kansa bugata da guduma ya lume tsakiyar kansa. Numfashi yaja me wani irin nauyi yana sake ambatar astagfirullah,daidai lokacin da yake bude idanunsa a hankali sai suka sauka kan fuskar omari dake tsaye cikin gurin wanda sam baisan sadda ya shigo ba. "Kada kacemin banyi sallama ba......don bansan jazabar daka shiga ba data hanaka jin kyawawan sallamata har guda uku" Ya fada yana daukan apple guda daya dake saman tray sannan ya koma ya zauna saman kujera gami da yin bismillah ya gatsa ya fara ci. Idanunsan nan ya zubewa omari yana maimaita abinda omari din ya fada. Banda babu 'yar qarya a tsakaninsu da kai tsaye zai qaryata omari din. Baiji wani sound ko daya na sallama ba ballantana motsinsa,kuma bayajin tunanin da yakeyi din yakai nisan da zai hanashi jin hakan. "Kana da baqo......na dakatar dashi ne akan saina shaida maka zuwansa in kana da interest na ganawa dashi" Omari ya fadi yana sake kai apple din bakinsa. Idanun nasa kawai ya watsawa omari da body language dinnan nasa dake nuna tambaya ga omari din. "Kaaiii" Omari ya fadi yana gotar da nasa idanun daga cikin na haisam. "Am telling you ka daina tsare mutum da wannan idanun naka idan ba qarya yayi maka ba,idan ba haka ba one day zaka saka mutum ma yayi qaryar,abdii yasha gaya maka hakan". Sassauta kallon nasa yayi kadan,can qasan ransa yana mamakin meye haka a idanunsa da suke yawan complain?. Shi kam zai iya cewa bai ganin komai koda ya tsaya ya kalla cikin mirror,abu daya ya sani,suna da girma,girman kuma daba me yawa bane can can,sannan wani lokaci sukan koma su rusuna kamar name jin bacci,musamman idan ranshi na bace ko kuma ya gaji sosai ko da gaske baccin yakeji. Bai cewa omari komai ba,ya miqe tsam yana ware hannun long sleeve black shirt din jikinsa dake nade tun dazun. Da kallo omari ya bishi sannan ya sake magantuwa. "Bansan a ciki wanne kaya bane sukafi maka kyau.....jubah?.....shirts da trousers?.....ko suit?" Yayi maganar da dukkan gaskiyarsa yana tallafe kanshi da tafin hannunsa guda daya. Kaman baijishi ba haka yayi,sai ya duqa kadan kaman yana dauko wayarsa,ya faki idon omari din ya hado da wata babbar apple guda daya,ya dago cikin hanzari ya jefi omari din da ita yana cewa. "Ban sani ba......wannan ta baka amsa dan neman rashin zaman lafiya,zan gayawa nanay,duk ranar da akace mayu sun kamani to tabbas cikinku ne kai da su amjad" Sosa qirjinsa inda apple din ta sauka omari keyi yana dariya bayan ya dauketa daga saman cinyoyinsa inda ta fado. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* Page 70 ____________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ "Ka tunamin da masoya......yau ya kamata mu hadu mu sada zumunci koda ta video call ne........amma dai gaskiya ce ba zamu daina fadi ba,ka rufa mana asiri ka fidda mata ko za'a samu kaifin kyan nan da abinda ke diban mutane ya ragu". "Saika aurar dani din ai" Ya amsa masa qasa qasa yana sauka da stairs din cike da karsashin nan nasa da cikakken kuzari irin ta lafiyayyen namiji. "Saura qiris.....menelik na nan,ga kuma saamee,auren gata,mata biyu a rana daya.....motii yafi daukan jikokinsa da yawa kuma da wurwuri.......don wallahi a idanunka naga duk matar daka aura zai wahala ta cika shekara daya babu d'a". Wannan maganar ta omari ta qarshe ta sakashi sakin murmushin da baiyi niyya ba. Omari yafi kowa shige masa hanci da qudundune,bai sani ba tsananin shaquwarsu ne ya kawo haka?. Yafi kowa gaya masa maganganu ire iren wannan gaba gadi,ba kunya ba shayi ko nauyin abinda zai fito daga bakinsa. Tabbas banda yanzun yana da abunyi me muhimmanci sai ya koma ya samu omari ya gaya masa wanne irin kalar sharri ne yayi masa haka?,amma ya saka maganan a mala,tabbas sai omari yayi bayaninta. Bedroom dinsa ya koma ya daura alwala,sannan ya tsane ruwan da towel,don yasan zai wahala kafin su gama ganawa lokacin sallah bai shigo ba. Babban minister ne harkokin tsaro na cikin gida,yasan da zuwansa,amma bai bashi daman zuwa din ba,bai kuma zaci zaizo koda bai samu izini daga gurin haisam din ba. Tunda ya riga yazo bazai qi ganinsa ba,don mutuntawa da martabawa suna daya daga cikin kyawawan halayen haisam din. Kafin ya fita ya dauki personal waya ya kira security kan su bashi masauki gashinan fitowa. Da wannan kwarjinin cikar haiba da kamala yake takawa zuwa inda ya bada umarnin a saukeshi. Tsam ya miqe wani irin kwarjinin haisam din yana cikashi tun kafin ya qaraso. Wani gefen na zuciyarsa kuma mamaki ne yake kamashi,a qalla ba aksar ba,ya haifi haisam din,bai taba zaton ganinsa yaro qarami irin haka da wannan babban muqamin ba. A shekarunsa ba'a taka matsayin dashi yake dashi cikin national security intelligence agency. Kai tsaye haisam ya bashi hannu shima ya miqa masa suka gaisa. "Bismillah" Haisam ya fadi yana masa nuni da mazauni cikin nuna alamun girmamawa. Abun ya burge minister sosai,akwai alamun tarbiyya da kuma ilimi me zurfi a tare dashi. Sai da minister ya zauna sannan shima ya zauna suka sake gaisawa kafin su fara tattaunawa akan dalilin zaman. Kusan duka tattaunawar tasu da harshen French ne......abinda yayi matuqar bawa minister houdu mainassara mamaki. Yadda yake sarrafa yaren saman harshensa zaka rantse haihuwar qasar French ne,harma yana so ya fishi qwarewa wajen furta yaren kaman shine da kuma haifaffe ga yaren. "Mun lamunce da zamanku......kuma zamu baku dukkan wata gudunmawa wajen kama wanda kuke nema,muma din zai bamu cikakken tsaro ai da kwanciyar hankali cikin qasarmu". Kai haisam yake gyadawa cike da nutsuwa. "Ma sha Allah.....a madadin gwamnatin qasar Ethiopia da shugabannin NISS muna miqa godiya a gareku da gwamnatin qasarsu,kuma in sha Allah zanyi qoqari a yau dinnan zanyi magana da His Excellency mr President,zan shaida masa goyon bayan da muka samu daga gareku" Murmushi houdu mainassara ya saki,haisam din yana sake burgeshi ya miqa masa hannu suka sake musabaha. Confidence dinsa da irin qwarewarsa,fasahar zance da yadda yake kowacce magana cike da nutsuwa suna sake kama hankalin mainassara. "Ina fatan zumunci bawai zai tsaya bane iya batun daya shafi aiki kawai" Minister ya fadi sanda haisam ya masa tattakin rakiya zuwa bakin motarsa guda daya da yazo da ita saboda kauda hankalin jama'a daga kansa. Murmushi haisam din ya saki,bai fahimci me mainassara yake fadi kai tsaye ba,amma with time yasan zai fahimta. "In sha Allah.....saidai kada ka sanyani alqawarin yin ziyara a tsakaninmu saboda yanayin aiki" Dariya kadan mainassara ya saki yana jinjina kai "Bazan sanyaka ba,har sai sanda ka gamsu da kanka,ko ni aka bani dama nazo" Kai haisam ya jinjina,ya kuma ja da baya da kansa yana rufewa mainassara qofar motar. Tare suka taka da omari suna komawa ciki yana gayawa omari din wasu daga cikin abubuwan da omari xai iya sani. "Mun kama hanya,inaji a jikina" Omari ya fadi,sai haisam ya gyada kanshi. "In sha Allah,komai zai tafi daidai". Lokaci ya duba sanda yake komawa daki,akwai sauran mintuna kafin ya fita agadez palace,don haka ya zauna ya soma lalubar number president na Ethiopia don bashi bayanan da suka dace,kafin nan kuma ya kira bobbo muhammad daud shima. President Amaan Mikel andom wanda haisam yayi saving number dinsa da Mr amaan. Daya daga cikin tsayayyun shugannin qasa a tarihin Ethiopia da qasar ta samu,jajirtattu da sukayi tsaiwar daka a kanta. Kasancewar masarautar jimma daya daga cikin masarautun dake da girma da qarfin iko.....kyakkyawan tsari na aiwatar da mulki da samarwa mutanenta ci gaba ya haifar ya kuma samar da kyakkyawan alaqa tsakanin gwamnatin qasar Ethiopia da masarautar. Uwa uba tsirowa da kuma samuwar jajirtaccen dan kishin qasa,qwararren ma'aikacin national intelligence and security service prinsii muhammad haisam cikin masarautar jimma,wannan ya qara zurfafa alaqa a tsakaninsu. Samun irin haisam cikin hukumar abune me wahala,matashi me ji da gata fikira kyau uwa uba ga sarauta a gefe,amma hakan bai hanashi jin sha'awar taimakaw qasarsa da dukkan fikirar da Allah ya bashi ba. Muhammad haisam din yayi ayyuka masu tarin yawa.....ayyuka masu zafi wadanda ba'a taba yin irin su a tarihin hukumar ba,wannan ya sanya sosai mr President Aamani yake ji dashi. Tun ba'a wani jima ba yaso hadashi da d'iyarsa,shalelensa wadda ita daya ce 'ya mace daya haifa wato HAANA amma a hankali da kanshi ya fahimci hankalinsa baya ta gurin. Duk da hakan bai sanya ya janye qudurinsa ba,yaci gaba da qarfafa alaqar zumunci a tsakaninsa da haisam,a tsakaninsa da masarautar jimma ta dukkan hanyoyin da suka dace,yana sanya ran watarana alaqa me qarfi ta qullu tsakanin haisam din da haana. *MOMMA* Daga waccan ranar har kawo yanxun da take tsaye gaban closet dinta bayan ta ciro wata alkyabba da aka samar da ita daga wani silk material me tsadar gaske tana sakata a jikinta......hankalinta da tunaninta gaba daya bai sauka daga kan akhnan ba. A kowanne rana tana sanyawa cikin sirri ana laluba mata halin da take ciki. Koda kebe kanta da tayi na wadannan kwanakin tana kwanciya ne ta kuma tashi da tunaninta ya take ciki?,me takeyi yanzu?,me yake gudana a kewayenta?. Koda sau nawa akhnan zata aikata laifi.....koda meye zatayi batajin zuciyarta zatayi nesa da ita,zuciyarta zatayi nesa daga soyayyar da take mata,wanda wani bangarene kawai na soyayyar safeena da tayi fiffike ta sauka a kanta. A nutse ta waiwaya tana duban falaak data shigo dakin da sallama gami da amsa mata sallamar,rungume take da litattafanta,wani kwantaccen murmushi yana fita saman fuskarta. Idanunta ta lumshe ta kuma budesu duka lokaci guda,a kwanakin nan wani nutsuwa da tarin walwala momma take hanga shimfide saman fuskar falaak din. Ga wata irin nutsuwa data sake fahimtar tana shigar falaak din,duk da dama ita din bame hayaniya bace ko zafi surutu ko rawan kai,saidai tana da kuzari sosai da hira ga duk wanda ta aminta ta kuma saki jiki dashi. Sake duban falaak din tayi,dukka yanayin dressing dinta yana sake canzawa,duk da dama can ita ba ma'abociyar shigar bayyana tsiraici bace,wannan din tarbiyyar hairaan ce......hairaan kuma rainonta ce,duk kuwa da cewa suna rayuwa cikin masu jajayen kunne,to amma wannan yanayin dake tattare da falaak na dabanne. Har a cikin ranta,har kuma zuciyarta tana jin cewa inama ace biftu ce ta samu dukkan wannan kamalar?,inama ace biftu ce ta samu wannan nutsuwar?,inama ace biftu ce ta samu wannan walwalar?. "Momma" Falaak ta furta a shagwabe,tana waving hannunta saitin fuskar morsa safiyya. "Momma wannan kallon kamar bakisanni ba?" Ta sake fada a narke. Murmushi morsa safiyya tayi,tana qoqarin maida hankalinta jikinta gami da soma gyara rigar jikinta. "Meye ne haka yake sauyamin ke falaak?,ko dukka karatunne?" Wani qawataccen murmushi daya qara bayyana kyan falaak din ya qwace mata,wata 'yar qaramar kunya da batasan me ya haddasata ba ta taso ta rufeta,saita matsa tana taya morsa safiyya gyara rigar jikin nata. "Ko dadin karatun sheikh muhammad dinne?" Morsa ta sake fadi tana fatan samun wani haske da zuciyarta ta jima tana haska mata shi. (08187255862 lu'u lu'u paying) Irin murmushin dazu ta kuma saki tana fara sawa morsa safiyya maballan rigar. "Nima ban sani ba momma.....kawai dai ya iya karatu gaskiya,yana da wani irin fasahar koyar da karatu,bani ba hatta badeea tace bata taba jin dadin karatu irin nasa ba.....momma ilimin dake kanshi da fasahar dake harshensa yafi qarfin koya karatu a gida......jami'a ya kamata ya tafi cikin dubannan dalibai.....momma har yanzu mamaki nake,jikina yaqi gamsuwa da cewa shi din gama garin malami ne kamar kowa". Shuru morsa safiyya tayi,tana jin yadda falaak din ta tsinke da surutu har fiye da bayaninma da momma din ta tambayeta. Murmushi ta saka me dan sauti,a hankali ta soma takawa. "Nagartacce ne kenan?" Momma din ta fadi ba tare data waiwaya ta dubi falaak ba,don batason ta bata haske akan wani abu take zargi. Tasan falaak sarai,tana da wani irin alkunya,tsaf zata tsinke zaren zancan ba tare kuma da ita takai ga gaci ba. Idanu falaak ta fidda waje tana qaramar dariya. "Momma......idan nace miki har yau sau daya tak ya taba kallona zaki yarda?" Har cikin ranta momma din taji mamakin abun,amma sai tace "Kaman yaya?,shi baya kallon mutane ne?". " Momma.....bama kallo kawai ba,ko magana sau daya zuwa biyu take hadamu har a gama karatun,idan kinga yana sake fuska to da aaera ne,don ko da Aafreen ba sosai ba.....na fuskanci yana da tausasawa da tausayawa ga yara,yadda yakewa aeera karatu daban da yadda yakewa Aafreen,nima yadda yakemin daban da yadda yakewa Aafreen,wani irin qasaitaccen murmushi yakeyi momma,saika lura sosai kake iya banbancewa.......me kyau dashi momma". "Halan ke tsira masa idanu kikeyi ko?,bayan shi kame ganinsa yake?" Maganan momma din kenan data dawo da ita hayyacinta. Bakinta ta rufe tana dariya gami da girgiza kai,sai a sannan taga kaman maganganun data saka sunyi yawa. "Aah fa momma.....idan zanyi tambaya ne ko shi ya tambaya wani abun,ko idan yana yiwa su Aaera karatu......" "Sai kita qare masa kallo kafin azo kanki kenan ko?". Wata qaramar tsawar kunya ce ta buga cikin kan falaak,kaman zata nutse a wajen. Ya akayi momma ta gano ainihin gaskiyar qarshen zancan?.....da gaske ne,tana yawan satar kallonsa idan suna karatu dasu Aafreen kafin ya sallamesu yazo kansu,amma daga nan bata iya sake kallonsa,saboda wani mugun mahaukacin kwarjini yakeyi mata,idan yazo musu karatu duk sai taji ya cika gurin da kwarjininsa,wannan qamshin da bata taba jin makamancinsa ba,hannunta har rawa yakanyi wasu lokutan,tana samun lalubo nutsuwar ta ne da zarar ta gama biya karatun jiya baice komai akai ba,alamun ta iya ba gyara ba kuskure. "Saura awa daya ku shiga aji,kinsan dokarsa ai ko?" Momma ta fada tana takawa don ficewa daga dakin,ganin falaak ta daskare a wajen ta kasa cewa komai. Saida tayi nisa sosai da gurin sannan murmushi ya kubcewa momma din. Ta soma tariyo maganganun falaak da kuma yanayinta. Tun daga sanda taga irin yabon da sultane yayi masa,da kuma daukansa a mazaunin mashawarcinsa na musamman taji dari bisa dari ta yarda dashi. Ballantan Aeera da kowanne lokaci cikin hirarsa take?. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* Page 71 _____________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ____________________________ Ajiyar zuciya ta sauke me nauyi,fatanta da mafarkinta a kullum shine,Falaak da akhnan suyi auren isa da qasaita.......idan tace hakan bawai tana nufin qasaitaccen namiji me kudi ba.....aah qasaitaccen namiji tsayayye isashe ma'abocin sanin haqqoqin matarsa akansa. Wanda zai tausayawa ainihin rauninsu na diya mace......zai riqesu bisa gaskiya da tsantsar amana.....koda rayuwa tazo da juyin da duk wani abu me daraja a tare dasu zai tafi ya barsu,kyau ne mulki nasaba ko dukiya?. Wanda bazai wulaqantasu ba bayan sun rasa dukkan wadannan abubuwan,wanda zai zame musu mijin HUCE HAUSHI......namijin kerewa sa'a da nunawa duniya gurin samun kulawa kariya da kuma riritawa. GARKUWA take nema musu a sanda duniya zata iya harar rayuwarsu.......DIRKA take nema musu a sanda duniya ke neman ruftowa saman kawunansu.......MAFAKA a sanda rayuwa zata iya kadasu kota hargitsa su. Indai ya zamana wani al'amari ya darsu a zuciyar falaak game da sheikh muhammad haisam.......lallai zatayu bacci cikin nutsuwa cikin rayuwarta,zatayi bacci harda minshari bisa samun tabbaci da yaqinin kyakkyawan zabin da falaak ta yiwa rayuwarta,saidai fatan ta samu kwatankwacin abinda take tare dashi daga gareshi. Amma can qasan zuciyarta zataso ace dukkan hakan ta kasance da akhnan. Hakeem kusan yana da wasu daga cikin qualities din daya sanya taji ta aminta da hadinta dame martaba......amma akwai abu daya da har yanzu yake tantama a kansa. Hakeem bashi da ZAFI bashi da ZARRA baida TSAIWAR DAKAN da take tunanin ita kadai ce zata bashi daman juya akhnan......ita daya ce zata bashi daman tafi da ita a sunan matar aurensa. Har a qasan ranta takejin kamar shi din BA JAJIRTACCE BANE.....irin jajircewar da take buqata take fatan ta kasance cikin jini halayya da dabi'un dukka mijin da zai zama mallakin akhnan din,domin sune abokan tafiyar iya zama da wannan TAURIN KAN nata,sune abokan tafiyar wannan KAFIYAR TATA. A wannan yammacin tana jin dukka dauriyarta ta qare,tana buqatar riskar akhnan din a inda take,ta zauna da ita,tayi maganan fahimta da ita,irin maganan da UWA zatayi da DIYARTA. Ta kusa da parlor din qarshe ta samu buhaina tana faman goge gogen falon da sassanyan turaren daya kama sassan,wanda anihinsa an samar dashi ne daga companyn INCENSE BY KABO DAUGHTER +234 803 211 9803. Wani turare ne na dindindin daya kama komai na parlor din. Tana tsananin son qamshin,amma ita kanta batasan daga inda ake samo turaren ba. "Ta fito dazun,ta zagaya ta wancan shiyyar qarshen sassanta" Buhaina ta fadi kanta a duqe da girmamawa. Kai morsa safiyya ta jinjina. "Buhaina" Ta kirata a sanyaye "Allah ya baki yawan rai". "Kuyi qoqarin riqe amana da kyau......ku kula da akhnan kaman yadda masarautar agadez ta yarda daku ta dauki amanar abu mafi soyuwa a ranta ta baku". "In sha Allahu......in sha Allah da dukkanin iyawarmu,sai inda qarfinmu ya qare" Ta fada cikin girmamawa tare da jin qarin qaunar matar da ganin darajarta me tarin yawa a idanunta. Awa daya saura lokacin karatu ya shiga ya qaraso cikin masarautar,ya kuma samu jagorancin me wada cikin girmamawa zuwa ga sashen guda da me martaba ya mallaka masa a duk sanda yake da buqatar zama. "Allah ya qara kusanci.....dukkanin gurin nan mallakinka ne halak malak muddin rayuwarka......ga osama nan......" Ya fada yanayin nuni da wani nutsatsen saurayi. "Me martaba yace abaka shi don yi maka dukkan wata hidima ta cikin gidan nan,kome kake da buqata kuma kana iya sanar dani,in sha Allah za'a samar maka dashi da gaggawa". Me wada ya fadi bayan ya gabatarwa da haisam kansa a mazaunin babban bawan dake da alhakin kula da hadiman dake da alhakin kula da sassannin iyalai name martaba,wanda a yanzun haisam ya shiga qarqashinsu. Koshi me wada yayi mamakin kawo haisam din kusa da villas din iyalin me martaba haka har kusa kusa,amma bayan kallon farko da ya yiwa haisam din,kwarjininsa ya cikashi ya kuma ga dacewa da cancantar hakan. Cikin nutsuwa ya gyada kai "Ina godiya,zan sanar idan akwai buqatar wani abu" "Na barka lafiya" Me wada ya furta yana juyawa gami da barin wajen. A nutse abdii wanda a yau ya samu nasara haisam ya taho dashi yake qarewa sashen kallo. Babban bangare ne da aka wadatashi da dukkan nau'in kayan alatu......saidai bai ko kama koda kwata kwata kwatar gidansu na nan cikin agadez ba.....ballantana har ya taka ya tsallaka ya kuma kai kimar sassan da prinsii haisam din yake mallakinsa cikin masarautar jimma. Kallon abun abdii yakeyi yana dariya qasa qasa,wannan shine daidai da karin maganar da yakan ji lokaci lokaci,ana cewa wai a rashin sani kaza ta kwana kan dami. Baisan adadin gidaje irin wadannan dama wadanda suka bigeshi a girma kyau da daraja ba da muhammad haisam ya badasu kyauta ga mutanen da basu da muhallin rayuwa ba,yana kuma kan bayarwa,don ko a tahowar nan tasu ana gab da kammala ginin estate guda me dauke da gidaje dubu da zai rarrabawa mutanen da basu da matsugunni,da kuma 'yan gudun hijirar da gwamnati ta yarda da zamansu. A yanzun aka saka masa bindiga baisan adadin gidajen da obbo din nasa ya gina ya bayar ba,gidaje kuma complete gida da furniture da komai,bawai kangon gida ba. "Gaskiya ne.....nan fa babban karramawa aka yi maka ko?......da gaske ne da akace qaramin sani qunqumi" Abdii ya qarasa fadi yana sakin dariya sosai,har yana fadawa saman daya daga cikin sofas din parlor din. "Abdii' ya kira sunanshi da wani irin tone da yaja hankalin abdii din,sai ya miqe ya zauna daga dariyar da yake qyaqyatawa. "Ka manta da rules dina?" Ya sake tambayarsa calmly yana shawagi cikin parlor din. Gaban wani window ya isa,yasa hannu ya yaye labulen ya kuma buda window din,take sassanyar iska ta fara shigowa ciki. "Afwan obbo.....bazan sake ba". Abdii ya fada cikin d'ari d'ari. Burinsa su zauna a nan din tare da haisam din,to ya tabbatar indai baiyi wasa ba kadan daga aikin haisam ya maidashi gida. Wannan ne kuma sam bazai iya haqura ko lamuncewa ba,qafarsa qafar haisam din,don bazai bar komai da zai cutar dashi ya rabeshi ba,zai zame masa kaman garkuwa ne koda obbo din baya son haka,zai riqe wannan amanar ta motii da nanay. Idanunsa ya sauke ta gurin,wani irin guri ne me kyau yake fuskantar gurin,wanda da ya duba da kyau sai ya fuskanci ginin benensa na sama akwai balcony na musamman da aka fiddata tana fuskantar gurin. Wani sirrintaccen murmushin qasaita ha kubce masa,kawai ya hango gurin da zai zauna ne yayi karatunsa cikin nutsuwa,sai ya maida window din ya rufe yana dawowa da baya. "Kana iya tafiya sai na nemeka" Yace da abdii kai tsaye. Idanu abdii ya fiddo waje yana duban haisam din. "Amma obbo......" "Shshshsh" Ya fadi yana dora yatsansa akan lips dinsa gami da zubewa abdii din idanunsa. Janye kallonsa yayi daga kan haisam din,ya karyar da wuya kalar abun tausayi sannna ya juya ya soma takawa. Har yakai qofa ya tsaya. "Ko kace na yafi zan dawo obbo.....Allah bazan iya zama can gidan ni kadai ba.....zan dawo,Allah obbo zan dawo" Ya qarasa fada da sauri yana fita a sassan don kada ma haisam din ya fadi abinda zai karya tsarinsa. Murmushi kawai yabi bayan abdii dashi,ya sani dama indai abdii ne saidai kawai yayi haquri ya qyaleshi,to amma dole ya kiyaye wasu abubuwa muddin zamansu yana so ya yiwu,dole ya ajiyewa abdii wani jadawalin tsare tsare. A nutse yaci gaba da bincike dukkan wani loko da saqo na sassan,yana kuma nazartar komai. Saboda qwarewa da yadda aikin sarrafa tsaro yabi jikinsa......ba wani guri da yake sauka hakanan ba tare daya karanci kimiyyar yanayi da kuma tsarin gini dana tsaron gurin ba. Kusan komai yayi masa,ba wani abu da yaji zuciyarsa bata gamsu dashi ba,don haka ya soma takawa yans fitowa da nufin karantar dukka farfajiyar dake kewaye da ginin kafin ya wuce zuwa makaranta. *AKHNAN* A qalla ta kusa mintuna goma Idanunta a runtse,tana kuma jin yadda iska ke wasa da gashinta daga hagunta zuwa damanta. (08187255862 lu'u lu'u paying) A yau cikin rad'in kanta taji buqatar fitowa daga sassanta zuwa wannan kebantaccen gurin,wani guri da yake daga baya kuma daga qarshen sassanta wanda yayi linking da sashen dake maqwaftaka da nata,sashen daya zamana ba kowa a ciki iya saninta tsahon sanda aka ginashi,don haka take matuqar son zaman gurin a lokuta da dama saboda akwai privacy sosai a gurin. Kowanne zaren tunani da kuma tarin lissafe lissafen mafita ne suke kai kawo cikin kanta. Mammina din dai,ita kadai lissafinta yake bata duk inda taje ta bugashi ta dawo.......ita daya ce mafitarta dake tafin hannunta. Hatta da mamminan an sanar mata zuwanta kusan sau hudu,amma taqi yarda a barta ta shigo ballantana ta samu damar ganinta,amma a yanzu zuciyarta na jaddada mata ita kadai ce dai zata isar da ita ga muradinta........MORSA ce kawai keda wannan matsayin,amma bata fatan abinda zai sanya ta roqi kowacce alfarma daga gurin morsa safiyyan har abada. Tun daga nesa data zuba mata idanu sosai,sai take ganin wani sashe na kamanceceniya tsakaninta da safeena dinta,abinda ya karyar mata da zuciya kenan,ya taso da wani irin yanayi me qarfi ya azashi saman zuciyarta. A nutse ta iso gabanta,duk da akhnan din taji alamun taku amma hakan bai sanyata ta bude idanunta ba,saboda ta sani,koma waye yake shigowa gurin cikin mutum biyu ne mafiya muhimmanci a rayuwarta,mammina ko sultane,wanda bata sanya ran zai tako inda take a cikin irin yanayi da suke ciki ita dashi yanxu. Tsaiwar takun ya sakata bude idanun nata a hankali,saidai kuma wadda ta gani din bata taba tsammanin ganin nata ba. Abinda tafi hasashe da tunanin zata iya aikatawa shine,ta miqe kawai ta matsa daga gurbin da matar ke tsaye,don ba wani dalili ko hujja na hada muhalli da mutumin dake adawa da dukkan wani jin dadi da kuma walwalarka......bashi da amfani musayar numfashi da mutumin da yayi sila ko sanadin shigarka wani qunci,saidai kuma komai ya sauya......wannan tunanin ya canza daga sanda idanun su suka gauraya dana morsa safiyya. Kallon kallo suka yiwa junansu,kowannensu abinda yake yawo daban a ranshi. Batasan me ya hanats tashi ba har zuwa sanda morsa safiyya ta tako a hankali ta zauna a gefanta. "Biftu" Ta kirata a tausashe,sunan da haruffan kuma suka sauka har cikin kunnen haisam dake takawa ta gefan farfajiyar a hankali yana duba wasu irin furanni da aka zagaye katangar gurin da aka samar da ita ta wannan bangaren da itacen bamboo masu daraja. Kadan yadan juya,amma fuskantar ba wani bane a gurin,murya ce daga can wani guri sai yaci gaba da abinda yakeyi din hankalinsa kwance ba tare daya damu da neman daga inda sautin yake ba. "Biftu.....me yasa zaki daga hankalinki har haka?,me yasa zaki nemi cutar da kanki akan abinda yake ibada ne?......biftu,ki kori shaidanin da yake miki saqa a mugun zare,ki yaqi baqin tunanin dake wahalar da kanki da kuma rayuwarki mana......ba ta inda aure yake qasqantar da darajar diya mace,face ma daga mata martaba da kima da yakeyi,koda bata samun dukka abinda tayi buri ko hasashe a cikinsa.......amma martabar wannan igiyar da darajar sunan AURE dake kanta kadai ya isheta girma da alfahari......don Allah biftu,ki kyautata zato a rayuwarki ta gaba.....kiyi haquri ki fahimci zahirin rayuwa.......muna buqatar ganin wanzuwar jinin safeena......muna buqatar zuri'ar safeena ta wanzu a doron duniya a doron qasa kaman yadda kowannenmu ya samu nasa rassan.......safeena ce kawai bata samu wannan ba.....ki tausaya mata ta zamu zuri'a mara yankewa,ba wanda zai mata wannan sai ke......ba wanda yake da wannan ikon a hannunsa yanzu sai ke......inda ahmad yana raye......dukkan fatanmu da burinmu zaifi karkata a kansa fiye dake,amma zuwa yanzu,duk wani me sauran FATA da BURI akan AHMAD ya gama sarewa,ya gama lullube babin taba wanzuwarsa a masarautar AGADEZ. Daidai da sultane bashi da wani sauran BURI ko mafarki a kansa.....ke dindai.....ke kadai ce yanzu duk wani burinmu game da zuri'ar SAFEENA" Morsa safiyya ta samu takai qarshe da qyar muryarta na rawar dake nuna bayyanuwar raunin nan nata dake da wahalar bayyana. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* Page 72 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ Idanu alkhnan din ta zuba mata,duban morsa safiyya takeyi fes kanta tsaye. Fata take.....so take ta tashi tabar mata gurin salin alin ba tare da tace komai da ita ba,amma a yanzu da takejin zuciyarta na cike da ita......tana jin a yau kadai data samu dama ta furzar mata da wani abu ko yaya ne......ta gwada mata bata buqatar wannan alaqar.....wannna dangantakar gaba daya,ahalin salsalar da nasabar dukka basu cikin buqatun rayuwarta da suka zame mata dole. "Karki bari zuciyarki da shaidan su raya miki komai........safiyya ce.....shaqiqiyar safeena......qanwa a gareta,qanwa mafi kusanci mafi shaquwa ga mahaifiyarki......kisa dukkan hankalinki da nutsuwarki a wannan karon na roqeki......ki karbi shawarata koda sau daya ne tak a rayuwarki,nayi miki imanin ba zakiyi dana sani ba......" "Wannan shine babban danasanin da zanyi a rayuwata irin wanda ban taba yinsa ba......" Ta furta da wani irin calmness,saidai kuma idanunta suna qaryata nutsuwar dake tattare da kalamanta. Wani irin shock morsa safiyya taji,tayi sak tana duban alkhnan duba na zallar mamaki. Duban da take matan sam bai sanya ta rusuna,ko taji bata aikata ba daidai ba,kota rage kaifin kallon da take mata ba. "Don Allah....." Ta motsa labbanta tana sake fadi da wani irin sanyi. "Don Allah wannan dangantakar.....wannan alaqar.....wannan ahalin na safeena......wannan dangin dukka bana buqatarsu,don Allah.....nima ina roqonku.....ni khadeejatul akhnan......a yau,a karo na farko cikin tarihin rayuwata,na karya record dina......ban taba roqar kowa komai ba.......ban taba tambayar kowa yayimim komai ba,amma a yau ina roqarki momma safiyya me laqabin qanwa ga mahaifiyata......ku janye ku kuma fita daga dukkan wani sabga daya shafi rayuwar akhnan ". Wani irin harbawa yaji wannan jijiyar dake gefen kanshi yaji tayi har cikin qwayar idanunsa. Harbawar da yawanci idan tayi to ba shakka ransa yakai maqurar baci. Da sauri ya jefar da furen daya ciro a qasa,wanda ya tsinko shine don ya tantance launin qamshinsa,jifarwar da zaka zaci kunama ya kama bawai fure ba. Idanunsa ya daga a hankali yana kallon katangar da yake kyautata zaton itace ta rabashi da ganinsu,yana jin yadda idanunsa ke masa zafi zafi. Tun daga sanda yaji fitar sunanta daga bakin matar da bai tantance wace ba......tun daga sanda ya fahimci yana jin maganganun wasu ne da zai iya yiwuwa sirrinsu ne da bai kamata wani yaji ba,ya qara kuzarinsa na duba dukkanin flowers din yabar gurin,don yasan zai wahala ya iya sake dawowa ya duba din idan yabar gurin,yana da abubuwa da yawa daya tsara cikin satinnan. "Calm down.....calm down" Ya samu wani sashe na zuciyarsa yana gaya masa,yana kuma ji har cikin kunnensa. "A'uzu billahi minash shaidanirrajeem......la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimeen" Ya furta yana ja baya a hankali yana qauracewa gurin. A hankali yaji yana dawowa saitinsa,ya soma tuhumar kansa kuma da rashin gaggauta barin gurin don gujewa jin abubuwan da zasu bata ranshi irin wannan. "Astagfirullah" Ya samu kansa da furta a hankali yana motsa kyawawan labbansa. Wani irin girgiza morsa safiyya tayi da wani nau'in madaukakin mamaki......kalaman akhnan a yau sai takejin sunfi komai yi mata muni a rayuwa......ba ita morsa safiyya kawai ba......dukkan family din DIOURI ta hada tace bata buqata?,wannan wacce irin mummunar illa mammina ta yiwa ahalinsu?. Tunanin yazo qarshe da wani irin tawagar hawaye cikin idanun morsa safiyya,saidai kuma cike da wannan sadaukantakar tata ta soma maidasu cikin cikin idanunta a hankali a sanda ta jiyo muryar mammina din tana shigowa gurin. "Biftu?......biftu??" Tana kiran sunan akhnan din da wani yanayi dake nuna hankali sam ba'a kwance yake ba,yayin data kafe bayan wanda take gani da kallo. Bata iya ganin fuska ko wani sashe na jikinta,face shimfidaddiyar rigar data suturta jikin morsa safiyya din.......amma already tun kafin ta fito zuwa nan din ta samu cikakken bayanin morsa safiyya din tana tare da akhnan din a madaidaicin kebantaccen lambunta. "Biftu?......wanne irin shashanci ne haka?,wacce irin wauta ce wannan kika aikata?,kinsan adadin dagin hankalin da kika sani?" Mammina ta furta tana dafa dukkan kafadun akhnan ba tare da tabar wata alama da zata gwadawa morsa safiyya cewa ta ganta ba. Iya wanzuwar mammina a gurin ya karya zuciyar akhnan gaba daya,sai takejin dukkan gatanta kamar ya dawo,sai takejin kamar matsalarta taxo qarshe,don haka ta sanya fuskarta jikin mammina din tana riqeta da kyau gami da sakin wani boyayyen kuka da mammina din kadai taji sautinsa ta kuma fahimceshi. JINI YAFI RUWA KAURI wata nau'in karin maganan bahaushe kenan,duk da bataga fitar hawayen ba......duk da bataga wani alama ba.....amma har cikin jininta taji fitar kukan daga zuciyar akhnan din. GANIN RAUNI a tattare da ita,shine abu na qarshe da baza bari idanuwan mammina su gani a tare da ita ba....KOMAI GIRMAN TSANANI....KOMAI QARFIN BALA'I,wannna ya sanya ta miqe tsam daga inda take zaunen tana jifan mammina da wani irin kallon da tsana da tsananin qiyayya ce fal shimfide a cikinsa. "Komai nisan dare gari zai waye.....komai nisan jifa qasa zai fado.....komai girman gona akwai kunyar qarshe. Jini yafi ruwa kauri......nasaba da gaurayar jini cikin tsatso da tushe guda ba wani abu da zai iya sauyashi.....duk duniya ba wani sinadarin da zai kwashe wannan tabbatuwar jinin nasabar ya sauyashi zuwa wani na daban" Ta qarasa maganar wani sassanyan murmurshi yana fita daga saman fuskarta,kai bakace baqar wuta ce ke zabalbala qasan zuciyarta ba a daidai lokacin. Zuzzurfan kallon kallo suka yiwa juna na wasu sakanni,sannan morsa safiyya ta juya a hankali tana takawa cike da nutsuwa take barin gurin,saidai ko mintuna daya tak batayi da bawa mammina baya ba,hawayen da take maqale dasu suka maye gurbin wannan murmurshi da tabbas tasan fake ne,na bogi ne......murmurshin da suka d'arsa wani qaqqarfan abu a zuciyar mammina.......ta kuma gaza dauke dubanta daga dukkan wani taku na morsa safiyya da daukeshi. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Na gode" Morsa safiyya ta fada a hankali labbanta suna rawa sanda ta shafo hawayen da yatsunta ta kuma bisu da kallo,sannna ta rab'e ta wani kebantaccen guri daya zama nata ita daya don ta rage nauyin dake qirjinta ba tare da kowa yasan da wannan ba. Ta godewa hawayen ne saboda basu bada ita gaban mammina ba......ta yaba musu ne saboda basu fita a sanda bai kamata su fita ba,ya kuma jinjinawa zuciyarta data iya dauke wannan nauyin me girma bata bari anga gazawarta ba har sai data kaucewa idanun kowa. Zare idanunta tayi daga hanyar wucewar morsa safiyya cikin jikinta tana jin tabbas akwai wani abu........cikin tsakiyar wannan murmurshin lallai akwai wani abu. Ba kowanne murmurshi ne yake kasancewa murmurshi ba.....kaman yadda ba kowanne murmurshi ne yake dauke da ma'ana ba,wani murmurshin fanko ne......wani saqo ne......wani kuma barazana ce,wani kuma yakan kasance gargadi ne.....batasan a wanne muhalli ko bigire zata aza na morsa safiyya ba. Cikin nutsuwar da iyakacinta saman fuskarta take duban akhnan,cikin dakin daya kasance babu kowa a ciki,daga ita sai akhnan din suna fuskar juna. Duban akhnan din take tana mamakin fitar hawaye haka daga saman fuskarta. "Biftu......" Ta kirata a tausashe,saidai akhnan din taqi barinta ta qarasa fadin abinda tayi niyyar fada din ta soma girgiza ma mammina kai "Wallahi mammina.......bazan iya jurewa ba,bazan iya aurensa ba.......baiyimin ba......bana sonsa!.....bana qaunarsa,don Allah,ki gayawa sultane......karkice zaki juyawa alqawarinmu baya" Ta fada tana kama hannun mammina din tana dubanta da dukkan wani hope nata. Shuru mammina din tayi,fuskarta da yanayinta suna suna nuna rashin gamsuwa da maganganun akhnan din. "Na roqeki mammina......na roqeki,a yanzun bani da wani fata akan kowa sai ke,bani da sauran yaqini sai a gurinki". " Amma biftu....kinsan yadda sultane ya dauki maganan hakeem da girma kuwa?.....ke kanki kin sani,shawarwarin morsa safiyya na days daga cikin shawarwarin da sultane kewa kyakkyawan riqo da gasken gaske?". Idanunta ta lumshe sannna ta budesu,tana jin wani irin matsanancin zafin morsa safiyya cikin ranta. Daga sanda taji cewa ita ke riqe da ragamar karbar baquncin baqonta,daga sannan tasan cewa ba wani al'amari kuma da zai kasance me kyau a tattare da ita. "Bana son koda jin sunan matar nam mammina.....ki daina kiramin sunanta" Akhnan ta fada da wani irin matsanancin kaushi cikin muryarta. A zahiri idanu mammina ta watso waje tana duban akhnan,saidai batakai ga fadin abinda zata fada din ba akhnan ta miqe "Basai kin sake kiramin sunanta a nan wajen ba,iya kiran sunanta a kunne na yana daidai da kiran gagarumar matsala ko rashin sa'a a tattare dani......shikenan mammina.......shikenan tunda ba zaki iya nema min alfarma gurin sultane ba......shikenan na tabbata cikakkiyar maras gata data rasa tsayayyar uwa.....na tabbata wadda tafi kowa rashin gata a duniya..." Ta fadi maganan tana dosar qofa. Tsam mammina ta miqe,sannan ta kamo hannun akhnan din ta jawota da baya. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 73 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX __________________________ "Indai ina raye baki rasa gatanki ba......indai ina raye kuma na shirya sadaukar da komai a kanki muddin hakan zai sakaki farinciki.....koda hakan yana nufin sadaukar da fahimtar junar dake tsakanina da sultane ne,zanyi iyakacin bakin qoqari na,har sai naga abinda ya turewa buzu nadi" Ta fada tana bawa akhnan tabbaci da yaqini da dukka idanun data zubawa akhnan din su. Wani irin abu akhnan taji yana sauka saman zuciyarta dangane da mammina din. Wata irin qaunarta me girma ta taso ta soma lullubeta,a duniya tana da masoyi sama da mammina kuwa?,anya mammina batafu sultane sonta ba kuwa?,wanne abu ne a duniya zatayi ta sakawa mammina da dimbin tarin tulin soyayyar da take mata?,wannan soyayyar bata da kama......bata da daidai,sai kawai ta fada jikin mammina tana rungumeta da kyau,itama mamminan saita riqeta tana dan bubbuga bayanta gami da fadin. "Calme-toi,tout ira bien". ★Tsaki ya sake ja sau adadin da baisan yawansa ba,sannan ya ture system din gabansa gefe yana murza tafukan hannunsa cikin na juna. A nutse abdii ya daga kai ya kalleshi,tunda ya shigo yakeson tambayarsa abinda ya tabashi yau amma yana tsoron saba dokokin da aka shimfida masa kafin ya samu ya aminta da qyar su zauna tare. Maher kawai ya zaba su zauna dashi cikin gidan,saboda shi din ya kasance kamar wani ido ne gareshi cikin masarautar,saidai kuma kaida fata abdii yaqi aminta ya fita,dole haisam ya barshi,bayan ya zauna ya jera masa dukkan sharuddan da abdii kansa tsaye yace ya amince,duk kuwa da cewa yasan ba komai bane zai iya bi ba a dokokin. Numfashi ya zuqa sosai yana fesarwa ta bakinsa "What wrong with you haisam?" Ya furta da wata murya da daga shi sai zuciyarsa kadai ke iya jinta. Sake lumshe idanunsa yayi,yanajin wani bacin rai kadan kadan yana lasar zuciyarsa. "Why she's so stubborn?.a silly girl.....ya akayi ta kasance d'iyar kamilin mutum me daraja da dattako irin sultane. "Yukhrijul hayya minal mayyit?" Ayar tazo cikin kansa. Numfashi ya sauke a ransa,yana ji a rayuwarsa bai taba jin wani abu da yaji sam baiyi masa ba,bai taba jin wani abu da yakejin haushinsa yana ginuwa cikin ransa ba irin yarinyar. Totally irin matan nan ne masu tsananin girman kai?.....rashin iya magana?.....masu jin cewa izzarsu gaban na kowa yake?. Tunda ya soma jin maganganunta bisa akasi,ba wani magana me dadi da yaji ta iya da wani,ba wani kyakkyawan lafazi data iya fiddashi daga bakinta. Ya jima baiga mace me tsaurin ido irin nata ba.....who's she?. Tambayar qarshe da ya yiwa kansa kenan wayarsa ta dauki sassanyan ringing dinnan nasa mara hayaniya da yawa,kafin yakai ga dagawa anyi knocking,sai abdii ya bude ya tafi budewa shi kuma ya daga wayar. A nutse ya kammala wayar,ya kuma ajiyeta a nutse yana duban abdii daketa kai kawo yana zube wasu riguna a gabansa. Da idanu kawai ya tambayi abdii din ba tare da yace komai ba,sai ya dawo ya zauna yana murmushi. "Me martaba ne ya aiko,yana gayyatarka cin abincin dare tare dashi nan da awa daya". Idanu haisam ya zuba masa a nutse,wani lokaci quruciya da wautar abdii tana damunsa,duk da tarin nutsuwarsa da kaifin basirarsa,to amma bai sani ba,kaman shi daya abdii din yakewa haka. "Hakan da kake yana sakani tunanin anya zaka samu gurbi kuwa a NISS?". Idanunsa gaba daya abdii ya zaro waje yana duban haisam din. "Captain obbo......" Yayi maganar yana kwantar da murya da alamun damuwa. Haisam bai daina kallonsa ba,sai ma girarsa daya dage sama yana duban idanun abdii din. "Inajin kaman za'a dauki kalar ma'akacin da ba'a taba dauka ba........" "......wajen iya aiki obbo" Abdii ya qarasa masa maganar da ba hakan yayi nufin qarasawa ba. Ido haisam ya rufe yana dafe goshinsa da tafin hannunsa. Kome zai cewa abdii xai sakashi doguwar magana ne a yanayin nan da sam shi bai shiryawa hakan ba,don haka ya yanke wancan maganar "Me kace musu?". " Kana godiya kuma zaka halarta in sha Allahu,kaga zamu shiga muga yadda yanayin nasu qarfin ikon yake.......ina duba maka rigar daya kamata ka saka ne" Yayi maganan yana daddaga kayan dake ajiye gaban haisam din. Sake duban abdii yakeyi,wanda yayi burus kaman bai gane ba. Zuciyarsa na sake jin qaunar yaron,ranshi kuma yana dariya can qasa da bata bayyana ba. Bilhaqqi abdii yana mantawa aiki ne kawai abinda ya kawosu agadez,bawai nuna qarfin sarautar da masarautar Ethiopia ke dashi ba,ba kuma sunzo bane don a girmamasu ko a basu girma ba,hasalima hakan na iya nakasta tasirin aikinsu. Maher ne yayi sallama,haisam ya amsa masa,ya qaraso cikin a nutse yana rusunawa cikin girmamawar da idan sun kebe ne kawai yake samun daman nuna masa. "Barkanka Maher" Ya amsawa Maher din a ataqaice wanda shima hankalinsa yake kan kayan da abdii keta dagawa. "Obbo......zaka fita ne?" Maher yayi tambayar a nutse yana zama. "Tambayeshi" Ya furta yana masa nuni da sashen da abdii din ke zaune ba tare da ya sake bi ta kansu ba,sai ya ture duka kayan gabansa yana miqewa gami da duba lokaci. Gayyatar tazo masa a bazata,kuma tabbas inda abdii ya fadi masa zai basu haquri ne. Ba kasafai ya fiya son a jashi cikin wasu alaqoqi ko dangantaka masu zurfi ba. Murmushi maher ya saki bayan abdii ya bashi amsar tambayarsa. Da gaske rashin sani duhu ne da bashi da kama,inda sultane yasan da waye yake tare,ko wannan apartment din daya ajiye haisam zaisan yayi babban kuskure. Girma qarfi da izzar masarauta baya jin akwai ya masarautar oromo koda cikin Ethiopia ballantana sauran qasashe,amma a iya sanin Maher,ba qaramin mutum bane sultane zaiwa gayyata irin wannan. "Da gaske sultane ya baka babban matsayi da bana tunanin a tarihinsa akwai wanda ya samu kwatankwacin haka......karkace ba zaka halarta ba obbo......amma abdii wannan kayan duka daka dauko maidasu zakayi" Maher ya fada yana dariya. Ya sani,sau da dama abdii din yana manta mission dinsu na shigowa agadez,girma da matsayin haisam yana bugar dashi ya manta da wannan. Yana takawa zuwa dakinsa yana juya maganganun Maher. Dukka maganganunsa suna kan hanya,hanya daya ce kawai zata kawo masa komai cikin sauqi,tunda dukka wani bincike da kuma signals sun basu hasken wanda suke nema yana rayuwa ne cikin daya daga cikin masarautun qasar niger,masarautar agadez kuma nada girman da zarginsa yasa yafi rinjaye a kanta. A nutse ya isa dakinsa ya tura ya shiga,idanunsa akan private patio din gaban ginin benen wanda baida wani wadataccen haske. Ma'abocin son zama ne shi a irin guraren nan,don suna bashi iska me kyau,suna kuma bashi damar warware tunanikan da suka sarqafe masa kwanya. Duqawa yayi ya dauki wani abu kaman Bluetooth ya,ya budeshi,sai ga wani abu ya bayyana kaman keyboard dan mitsitsi. Wasu number dake bada kalan sky blue ya danna jikin qaramin Keyboard din,sannna ya zari Bluetooth daya ya cusa cikin kunnensa,ya maida dan qaramin box din ya ajiye ya fara takawa a hankali zuwa private patios din,don bai samu shiga gurin ba sam tunda ya fara zagaya sassan nasa. Fes gurin yake a tsare da wani irin tsaftar da ba zaka dauka saman bene bane. Lullube da wasu irin marbles masu daraja da sheqi. Glass ne ya zama kaman Katanga na gurin,wannan shine zai bawa wanda yake ciki cikakken daman ganin hagu da dama da kuma gaban komai dake zagaye da sassan nasa. Straight idanunshi suka sauka ga qawataccen ginin dake gabansa. Wani madaidaicin gini da yafi kama da gidajen da aka dauko cancakat daga qasashen turawa akazo aka dasashi gaban nasa. Daga yanayin color na paint din ginin,yawan deco na flower da ya hanga,da kuma tsarin private patios din dake kallon nasa ya tabbatar gurin mallakar macace. Akwai qarancin hasken dake nuna ba kowacce fitila bace ta sashen a kunne,kaman yadda farfajiyarsa ma bata cika haske sosai ba. Maida dubansa yayi hannun hagunsa,daga can din wani guri ya hanga daban,wanda da alama kebantacce ne shima,ba gurine na mu'amalar mutane ba,a yadda ya nazarci gurin yafi masa kama da wani guri na ajiye ajiyen kayan da ba nan kusa ake tabasu ko ayi amfani dasu ba. Hannun damansa ya maida dubansa,daga can nesa shima wani muhallinne na daban,sai ya janye idonsa a nutse sanda muryar omari ta cika kunnensa da cikakkiyar sallamarss. Ya motsa labbansa a nutse yana amsawa omari din sannan ya fara takawa yana dawowa bedroom dinsa gami da maida qofar da labulen daya raba tsakanin dakin da private patios din yana rufewa. "Mr ilaalcha gadi buusuun.......ya kakeyi da 'yammatan masarauta?" Omari ya fadi da sigar tsokanar nan tasa. Ido haisam ya lumshe sannan ya bude duka lokaci guda. (08187255862 lu'u lu'u paying) "Ka adana yaren oromo omari.......ba yanzu ba,ka saka a kanka kuma,shi muhammad haisam idan aiki ya taso masa,baya gane kowa,baya kuma gane komai,har sai ranar daya kammala aikinsa.....koda ya kammala dinma,nanay kawai yake ganewa" Ya fada calmly,kuma har cikin zuciyarsa yana jin hakan. Aikinsa nada matuqar muhimmancin da yakejin bazai iya hadashi da kowa ba,bazai kuma iya badashi da komai ba. Qaramin dariya omari ya saki,halayen haisam nada abun mamaki,sun jima a tare,amma har yanzu yana kan shan mamakinsa idan yayi wani sabon abu cikin halayensa da shi baisan dashi ba. "Naga alama.......ka dole Menelik sai data kirani,sai data nemeni da tarin jin kunyarnan taka,tana cigiyarka,gidanka satittika da dama ba haske,bata ganin motsinka kona wani a cikin gidan........ba zaka duba ba haisam kuwa?,anya?" "Omar" Ya kirashi cikin qosawa da maganganunsa. "Kaji da ita mana?.......saamee Menelik dukka nabar maka,kaidain mijin mace hudu ne ko?". "Haisam mana...." Omar ya fadi da zummar jan hankalinsa,da gaske tausayinsu yakeji,don shi kansa baisan ta hanyar da zamu cimma burinsu akanshi ba,daga ita har innocent saame. "Look please........muna bakin aiki ne ka tuna.......duk wani kira da zaka sameshi daga gareni ta wannan device din me muhimmanci ne,baida alaqa da kowacce yarinya........my rules are as simple as ABC......ya kamata ka haddacesu haka" Yadda tone din muryarsa ya canza ya tabbatarwa da omari da gaske yana nufin abinda ya fada. Murmushi me sauti ya saki yana jinjina kai kaman haisam na gabanshi. "Bana tunanin kana lafiya haisam......even little akayi magana akan abokiyar rayuwa "Omaaarrrrr...." Ya kirashi yana jan sunansa da qarfi,don attention nasa kawai yake buqata,wannan zancan ya isheshi haka. "I'm focusing on what matters most to me" Ya fada yana zuqar numfashi da yakejin kaman bazai kai masa ciki ba. Shuru ne ya ratsa tsakaninsu,omar yana sauraren saukar numfashin haisam din,yayin da shi kuma haisam ke qoqarin daidaita nutsuwarsa. "It's fine......idan lokaci yazo maka a qurace,zanga wadda zaka damqo,Allah ya rabaka da makahon zabe". Hannunsa ya aza saman kansa yana yamutsa lallausan gashinsa,da gaske dai dole omar wannan kafiyar tasa ba zata barshi ba.....dole sai ya qarasa zazzage masa abinda ke cikin ranshi?. "Zan shiga gurin sultane yau" Ya fadi saqon kawai kai tsaye,don maganganun omari kawai yana kallonsu ne a wasu abubuwa da basu da muhimmanci ko amfani face bata lokacinsa kawai. "That's good......da sauri haka?" "Out of the blue........yanzun nan saqon ya sameni.....inaso ka zama a ankare,this could be our starting point". "Yes" Omari ya fadi yana tashi daga kwancen da yake. "Any update from beeno?" Kai omar ya girgiza. "Munyi waya dazun,kowa dai yana bakin aikinsa........salawi ya tura wani information,ina cikin dubawa ne ma kiran Menelik ya shigo min". Tsaki yakeso ya jawa omari,amma ba abu bane me kyau,don haka yayi banza dashi kaman baiji ba. " Ka turamin ta office email dina.....ka kula gurin tura komai" "Wrapped up" Ya amsa masa,sai ya sanya hannu ya zare Bluetooth din yana katseshi gudun kada omari din ya sake jefo masa wani maganan. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 74 ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ A nutse ya matsa zuwa inda towels dinsa suke maqale,ya zari babba guda daya me tsananin laushi ya ajiye saman dressing table,ya soma zare rigar jikinsa,wanda hakan ya bawa faffadan qirjinsa dake dauke da lallausar gargasa daman bayyana. Wani irin baiwar suma Allah yayi masa,tun daga saman kansa zuwa kumatunsa habarsa girarsa,hannu da qafansa da kuma qirjinsa wanda ya hade har qasan cibiyarsa. Ba kowa ke fahimta ko sanin hakan ba,kasancewarsa ma'abocin sanya long sleeve shirts da kuma jubah masu dogon hannu da kuma rufaffen wuya. Daura towel yayi a qugunsa,yana shirin wucewa toilet still wayarsa ta tsaidashi. Ringing ne na musamman,wanda ya sakawa nanay. Sautin da ko bacci yakeyi idan ya jishi sai ya farka,don kirane na musamman daba kiran daya kaishi muhimmanci a gurinsa. Zame towel din dake fadarsa yayi sannan ya dauki waya ya jawo stool ya zauna,don indai kaga ya amsa wayar nanay ko motii a tsaye tabbatar hakan shine option din kadai daya rage masa. Cikin cikakkiyar nutsuwar nan tasa ya yiwa nanay sallama. "Wa'alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu" Ta amsa da cikakken sallama,wani sanyi na sauka qasan ranta,yayin data aza idanunta saman fuskar saame wadda ke takowa a hankali zuwa ciki tana dauke da wata irin royal burner da turaren wuta ke fita a hankali. "Barka da dare nanay" Ya fadi yana rusunar da kansa cikin yaren oromo kamar yana gabanta cikin tausasa harshe irin na 'ya'yan da sukasan tsantsar darajar mahaifiya. "Barkanka da wannan lokaci muhammad......" "Kina lafiya?......" "Alhmdlh muhammadu" "Motii fa?,na gaza samun wayarshi tun jiya,nayi magana da hussam nace ya hadani dashi". Murmushi kadan nanay ta saki,tasan akwai daru yanzun nan. "Motii baya masarauta,yayi wata 'yar tafiya" Idanunsa yadan qarawa girma kadan kamar nanay na kallonshi. "Nanay?,zuwa ina?,ina kuma yaje?". Ya furta calmly,saidai kuma muryarsa tana nuna labarin bai masa ba sam. "Ba wani guri yaje ba,umara ya tafi,sati biyu kacal zaiyi ya dawo,shi ya hana a gaya maka saboda yasan zakace ya jiraka,zaka baro aikinka ne ka dawo kuje kuyi tare ku dawo tare,yace zuwa yanzun ya kamata kaima ka huta,ya kamata ka tattara hankalinka gaba daya akan aikinka.....iyali zaka ajiye nan gaba kadan,bazaiyiwu ka hada hidimarsu da tamu ba". Wani sassanyan ajiyar zuciya ya sauke,wanda duk yadda yakai ga boyewa nanay ta jita cikin jikinta. Yana daya daga cikin dalilan da ya sanya yaji har yanzu batun maida hankali yayi aure sam bai zauna masa ba,baya qaunar abinda zai nesantashi daga hidimar kula da lafiya da duk wani motsin motii ko nanay. Akwai wata lullubabbiyar qura cikin rayuwarsu,qurar daya tabbatar har yanxu ba'ayi ruwan da zai daketa yadda ya kamata ya kwantar da ita katitir ba. Yayi imanin wannan qurar tana kwance......zataci gaba da kwanciya ne har zuwa ranar da zai damqo makashin ajani......ranar da duk wani da yake da hannu cikin mutuwar ajani zai bayyana,yana tunanin daga wannan lokacinne kadai yake da cikakken sukuni cikin rayuwarsa. Har yanzu basusan siradin da suke ciki ba,motii ma da ya fuskanci kadan daga ciki har yanzu bai dauki abun da girman daya kamata ya daukeshi ba,yana yaiwata gaya masa. "Muhammad..... Mutuwa da rayuwa dukkaninsu a hannun Allah suke,ba me rayawa sai shi,kaman yadda ba wanda ya isa ya kashe saishi". Ya sani,kamar yadda shima motii ya sani. Yana da dukkan wannan........amma hakan bazai zama hujjan da zai saki jiki ga kulawa da bada dukkan kariyar da zai iya ga halittu guda biyu mafiya daraja da kima a tattare da rayuwanshi ba. "Muhammadu?" Nanay ta kira sunansa a hankali,sanda saame ta qaraso gefanta ta tsugunna tana ajiye kaskon hannunta,ta kuma motsa zuciyarta na tsananta bugawa da zummar tashi tabar gurin. A tausashe nanay ta riqe hannuwan samee cikin nata tana kuma sauraren qorafin haisam. "Don Allah nanay......ki fadi masa,kada ya sake zuwa ko ina shi daya,yayi haquri har sai na dawo,idan ya zama dalili ne kuma na gaggawa,zan bar duk abinda nakeyi,zanyi booking flight nazo na daukeshi muje mu dawo" Murmushi maras sauti ya subuce mata. A duniya idan tace bata taba sani ko ganin iyaye 'yan gatan 'ya'yansu ba ita da motii batayi qarya ba. Bakinta harshenta dama zuciyarta gaba daya basa gajiya da nanata addu'a a kanshi da 'yan uwanshi,ba shakka tana cikin jerin sahun mata da sukayi dacen samun 'ya'ya a duniya. "Zan shaida masa in sha Allah.........nayi nayi da hussam yayi magana dakai akai kudaden daka saka ya sanya a account dina?". Sai daya sauke ajiyar zuciya kadan,har yanzu hankalinsa yana tare da mootii sannan ya amsa mata calmly. "Naki ne nanay,kiyi duk yadda kikaga dama dashi". Ba wani abu bane sabo a gurin nanay,amma yawan nauyin kudaden suna sanyata jin kamar tana shiga haqqinsa da yawa. " Jinan Muhammadu......kasan nawa ya saka?". Kai ya gyada a nutse yana lumshe idanunsa. "Na sani nanay.....ko kaina na saka aka narka aka saka miki a account dinki ban biyaki da komai ba......ba abinda na mallaka ba,ni kaina sai yadda kikayi dani" Ya fada da wata irin cikakkiyar nutsuwa dake saka masa wani irin kwarjini a fuska da nutsuwa a maganganunsa. Shuru nanay tayi na dan lokaci,tana jin kamar a duniya babu wani aiki data taba yi wanda ta cancanci ubangiji ya bata yaro irin muhammad haisam din,kawai baiwa ce da falala daga ubangijinta. "Allah ya farantawa rayuwarka,ya sanya haske daga farkonta har qarshenta,ya sanyaka cikin mafiya alkhairi kuma mafiya rinjaye a rayuwa". "Allahumma ameen" Ya fadi yana jin a duniya yau dai duka baiji wani lafazi mai dadi sama da wannan ba. "Shi da waye da waye suka tafi?" Ya dawo da zancan motii,abinda ya sake haifar da murmushinta tana jin hannuwan saame dake cikin nata har yanzu yadda sukayi sanyi qalau. "Shi da Musayyib da Hezbollah,akwai security da NISS suka aiko daga muhammad Dawood". Kai ya jinjina yana jin ya samu 'yar qaramar nutsuwa. Abba Dawood din yasan komai da zai sakashi nutsuwa a aikinsa,ya tabbatar shi yasa ya hada motii da security team. "Ga samee" Ya tsinci muryar Nanay cikin kunnuwansa. Ko kafin yace wani abu,ta cire wayar daga kunnenta tana miqawa samee idanunta akan yarinyar. A daren sam batayi niyyar kiran haisam ba,sai gobe kaman yadda suka saba. Amma hakanan take lura da motsin yarinyar ya sauya,ta zama so silent,bata da wani karsashi. Ta sani,tana kewarsa ne wanda alkunyarta ya sanya ba zata iya fadi ba,tsaron kima da martabarta kuma ba zata bari ta kirashi ki tsaye ba,saita miqe a nutse bayan ta damqa mata wayar,don sam bata da wani ciwon qafa ko nauyi jiki irin na wanda shekarunsa suka fara tafiya,ta taka a nutse tana bar mata dakin hutawar zuwa ainihin nata dakin kwanar. Daskarewa jinin jikinta yayi na wucin gadi kafin ya narke yaci gaba da kwaranyawa cikin jikinta da wani irin matsanancin bugun zuciya,ta maqala wayar a kunnenta tana jin kamar zuciyarta zata fito ta bakinta. Da wani irin sanyi da tsoro tayi sallama,yana jin yadda zuciyarta ke bugawa a qirjinta saboda tsananin kewarsa da tayi. Sanda ya amsa sallamarta kuwa saida numfashinta ya tsaya na wucin gadi,ta kuma gaza cewa komai,har sai da taji yace. "Kina lafiya?". " Alhmdlh obbo.... Ya aiki?,Allah ya taimaka yayi jagora". "Ameen ameen" Ya amsa mata a taqaice,don yana jin kamar tana cinye masa lokacinsa. Shurun data sakeyi sai yaji kaman bai kyauta ba. Yasan meye a zuciyarta,yasan kuma me take yaqi doshi,ko yaya tana buqatar abinda zaiyi calming nata down,koda bame yawa bane,don haka cikin qarfin hali ya tattara kalaman. "Komai lafiya ko?" "Lafiya qalau alhmdlh" "Ma sha Allah......ki kula da kanki,Allah ya taimaka". Saura qiris garin jan numfashi ta hada harda zuciyar dake qirjinta. Karo na farko da irin wannan kalmar ta fita a bakinsa zuwa gareta. Ta sani,he was a caring person......yana da tausayi musamman ga mace,amma bai taba gwada gaya mata kalma irin haka ba,sai kawai ta kifa fuskarta saman cinyoyinta zuciyarta na wani irin bugu,ko kalaman NA GODE da zuciyarta ke bata shawaran gaya masa bata samu damar fadi ba,don dama yana gama fadin hakan ya yanke kiran. "Har kun gama wayar?" Muryar Anani ta ratsa kunnuwanta. Kanta ta daga da sauri suka hada idanu da Anani din,sai ta kashe ma saame idanu tana dariya qasa qasa. "Muddin kikace zaki fara narkewa da soyayyar captain obbo......na rantse nan gaba zaki koma tamkar ruwa ne.......ni nasan irin su captain sheikh..........saamee...." Sai kawai Anani ta gaza qarasawa tahau girgiza kai. Ranar data fara duba daya daga cikin rubuce rubucensa akan soyayya,cikin wani irin tsari na a addinance yadda zaka kama zuciyar mace tabbas banda yayanta ne uwa daya uba daya tayi imanin ba abinda zai hanata fadawa soyayyarsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Wasu irin kalamai da aka shiryasu da harshen larabci,sannan akayi translating nasu da yare biyu English da oromo,sai da tayi kwana uku tana duba littafi daya,daga qarshe data fuskanci idan batai wasa ba littafin zai iya sauketa daga karatunta daga qwallafa rai zuwa bigiren fara soyayya ba shiri,saita lallaba ta maida masa littafin sa ba tare da yasan daukowar da mayarwar ba,wanda yana dab da gama rubutunsa yayi publishing nasa aikin tafiya agadez ya tsaida komai. Har yanzu idan ta kalleshi kalaman take gani saman fuskarsa. Wannan miskilar fuskar da babu fara'a murmushi ko sakewa a cikinta,fuskar da baki samun cikakken kallo daga gareta,da wadannan idanun masu wani irin nauyi,ashe sunsan tasirin soyayya har haka?. Kasa cewa komai saamee tayi da tsiyar da Anani ta sakata a gaba tana mata,illa dai ta miqa mata wayar nanay kawai ta wuce dakinsu,don idan ba haka ta yiwa Anani ba tabbas zata uzzura mata ne kawai. Saman gadonta ta fada,ta kuma jawo pillow ta rungumeshi sosai cikin qirjinta. Ba ita kadai ba,tasan akwai tarin tulin 'yammatan da suke cikin irin wannan yanayin saboda shi. Tayi imanin a duniya ba macen da zata ganshi taji baiyi mata ba,saidai idan dama tasan ba zata samu bane. Babu wata halitta da zata kasa qaunatarsa,yana da wasu irin halaye da qualities masu tsananin tsadar da yake nasarar sace zuciyar duk wanda ya mu'amalanceshi. Hatta da qannaneshi sonshi suke,saidai su za'aci soyayya ce irin ta 'yan uwantaka,saidai duk da hakan tsakanin hussam da Aarif ba wanda ya samu irin soyayyar da dukkaninsu sukewa Muhammad haisam din. Numfashi taja sosai cikin hunhunta. Idan tana imagination na ranar da zai kalleta yace INA SONKI SAAMEE,tana jin komai ya tsaya mata,ta kuma tashi daga wannan duniyar zuwa wata. Idan tana hasashen ranar da zata zama mallakinsa,sai taji kaman duniya gaba daya tata ce ita kadai.......to amma wanna fargabar tana nan. Wannan alwashin yana nan,batajin kuma akwai abinda zai canza shi. Tana buqatar ya gamsu da soyayyarta da kanshi. Tana buqatar suyi exchange na soyayya,bawai ita kadai tayi dakon soyayyarsa ba. Tana babban mafarki da buri na auren namijin da duk duniya itace burinsa......itace zabinsa,itace mafarki da dukka muradansa. Koda ita batajin hakan,idan ta samu wadancan abubuwan a tare da namiji.....zata yarda zata aminta ta rayu dashi,wataqila nan gaba zuciyarta ta cika fal da soyayyarsa kamar yadda yake mata. *MAMMINA* Yau da kanta ta shirya kanta a daren da zuciya da qirjinta ke cike da tarin lissafe lissafe da burace burace. Wannan zuwan,wannan tafiyar da zatayi da buqatar akhnan zuwa gaban sultane......a zahirin aiken na akhnan ne zallah.......a badininsa kuwa,wani babban buri ne......wata babbar buqata ce da take da burin cikarta fiye da girman buqatar da akhnan din keda ita. Hannu ta sanya ta jawo jewelry organizer dinta tana laluben abun hannun da zata sanya,wanda zai dace da yanayin shigarta. Har hannunta ya tsallake kansa,sai kuma ta dawo da baya tana sake sauke idanunta a kanshi,ta miqa hannunta ta dauka. Wani irin bangul ne na asalin kayan gargajiya me tsananin tsadar gaske. Banguls din qwaya biyu ne rak,suna tuna mata wasu abubuwa masu nauyi da suka shude cikin rayuwarta. Suna da wani tsohon dadadden tarihin da babu ranar da zata dora idanunta a kansu ba tare da sun dawo mata da komai ba. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 75 ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX _____________________________ Sultane yana sonsu qwarai........duk kuma da son da yake musu takan jima bata sanyasu ba,amma a yau din sai taji zuciyarta ta cika da sha'awar sakasu,ta daga hannun damata ta zurasu a nutse tana sakin murmushi ganin yadda ya sake qawata hannuwan nata. Tana maida jewelry organizer din taji an murda handle din dakin,kafin ta waiwaya kuma motsinta ya gaya mata ko wacece. A hankali cike kuma da mamaki ta juya tana dubanta. Akhnan ce,sanye da wata farar Malaysian Avaya. An mata wani irin kyakkyawan ado da gold din zare daya sake fidda kyau da qawatuwar rigar. Maqale mayafin rigar yazo a kafadarsa,kuma iya shi kadai akhnan din ta yafawa kanta,wannna ya bawa gashinta me sulbi dake kwance a agadon bayanta daman bayyana saboda wuyanta a bude yake saboda yadda tadan dora mayafin kawai ba tare data wani daidaitashi saman kanta ba.......hakanan kana ita gabin baqar sumarta data fara daga gaban goshinta,ba wani cirewar gashi kaman dasashi akayi. Wani irin kyau tayi,kyan daya dauki hankalin mammina ya kuma tuna mata da ranar farko data fara ganin SAFEENA a rayuwarta,ranar da har yau har kwanan gobe ba zata taba gogewa daga cikin kundin rayuwarta ba......ba kuma zata taba gogewa daga jerin sahun ranakun qaddararta ba. Idanunta ta lumshe tana controlling emotions dinta. "Ya akayi biftu?" Ta kirata da wani nau'un tausasawa cikin muryarta,tana duban fuskarta da tayi fayau tadan fada kadan,saidai hakan kuma sai ya zame mata kaman ado ya qawata shape din fuskarta lips dinta da hancinta gaba daya. "Zan biki.....zanje na roqu sultane da kaina......" Ta fada da salon miskilancin nan nata da yau ya nuna muraran. "Me yasa?,baki yarda da zan iya samun nasara a kanshi ba da kaina?" Kai ta girgizawa mammina,tana zama a sanyaye gefan sofa bed. "Bana tunanin a duniya akwai wata halitta mafi soyuwa a ran sultane.....halitta mafi daraja,halittar da tafi qarfin yayi mata kalan kowacce alfarma kamar ni,idan zaiyimin zai iya yiwa kowa......idan bazaiyimin ba bazai iya yiwa kowa ba.....na duba littafin da mahaifiyata ta barmin yau a karon farko,a shafin farko kadai dana duba kuma na fahimci haka". Idanu mammina ta janye daga kan akhnan,tana son tuna wanne littafi ne wannan da ita ta mance dashi?,wanne littafi ne da ita bata mallakeshi ba?,wanne littafi ne haka daya halitta mata sabon tunani cikin qaramin lokaci. Tattara komai tayi ta hadiyeshi tana sake jinjina kai. "Gaskiyan ki ne,mu tafi tare,yana da kyau" Ta fada tana miqawa akhnan hannu,ba tare da tayi qasa a gwiwa ba ta miqawa mammina din itama cike da fatan tabbatuwar nasara. ★Cikin shigar cikakken qasaitaccen basarake yake zaune cikin parlor din nasa,sanye da tufafin zaman gida,saidai kuma duk da sun kasance na zaman gidanne,amma na dabanne dake dauke da tambarin qasaita,tun daga yauqin da yadin yakeyi zai gaya maka tsadarsa da darajarsa. A nutse ya dauke idonsa daga saman tanqamemiyar Tv din dake aiki,wadda yake kallon labarai daga tashar France 24 dake haska labaran duniya ya maida ga bakin qofar yana amsa sallamar nutsuwarsa da kwarjininsa yana tasowa. Wani abu ne ya sauka zuciyar mammina,ganin yadda ya zuba musu ido a nutse yana kallonsu ita da akhnan din,yayin da kwarjininsa ya daki idanu da zuciyar akhnan din,har ya sanya ta motsa kadan tana lafewa a bayan mammina. "Barka da warhaka bajimi namijin zaki" Ta fadi tana sauke wani sassanyan murmushi saman fuskarta. Martanin murmushin ya maida mata,yana kuma dauke idanunsa daga kan akhnan dake takowa kaman wadda ke takawa wani abu me santsi da take tsoro kada ta zame. "Barkanki......barka da warhaka giwar agadez" Ya amsa mata cikin ransa zuciyarsa na ayyana masa komai kafin takai ga cewa ko aiwatar da komai din. Saidai har qasan zuciyarsa yana sake jaddadawa kansa,indai abinda ya shigo da ita kenan zaya basu mamaki su dukansu. Yadda ya maida mata kirarin ya mata dadi sosai,ya kuma sake qara mata qwarin gwiwa,sai taci gaba da takowa har zuwa daura dashi. Gefen mammina ta zauna,tana rabewa sosai a jikinta,kamar qaramin yaron dake bala'in qyuya yake kuma tsoron kada a tabashi. "Barka da wannan lokaci toron giwa......ina fatan za'ayi mana uzuri,za kuma a bamu dama,don zamu shiga lokacinka kadan". Idanunsa ya dauke daga kan mammina din,yana sauke basaraken murmushin nan nasa dake qara masa kwarjini,ya gyara zamansa sosai cikin tattausar sofa din da aka sake shimfida wani tattausan abu a samanta saboda nuna girma da martabawa ga wanda zai zauna akai din. Qaramin numfashi ya sauke dake nuna dattijantaka. "Bawa iyali lokaci ai abune dake da matuqar tasiri da kuma alfanu,saidai kawai ina fatan lokaci ya zamana an qarar dashi akan wani abu dake da tarin muhimmanci". Ba jiya ko yau aka raini harshe da kwanyarta ba,ba kuma jiya ko yau take zaune cikin yankin agadez ba ballantana ta gaza fahimtar harshe da kuma sigar daya watso maganganunsa akai ba. Sai ta jinjina kai,tana sake lanqwasa kanta cikin yanayin da tasan yana matuqar sassauto mata dashi a duk sanda yahau wani tudun naqi din nasa. Dukkan wani siffa da yanayi da tasan yana karya mata sultane din......dukkan wani yanayi da tasan yana mata jagoran samun nasara tattare da sultane din......gaba dayansu ta aro ta lulluba saman fuskarta . Wani yaqi ne da bawai ya shafi akhnan bane kai tsaye......a badini ma wannan yaqin.....wannan zaman nata ne....duk wani alfanu dacewa ko kuma hasara da faduwa da za'a samu NATA NE bana AKHNAN bane,akhnan ce kawai a fuskar,amma a lullube......a bayan fuskar a bayan manufar MURADANTA ne a shimfide. "In sha Allah.....ba zakayi dana sanin bamu lokacinka ba.....kuma nayi imanin zaka sauraremu da dukkan kunnuwanka masu cike da adalci da tausayawa na qasa dashi". Motsawa ya sakeyi kadan yana lanqwasa yatsunsa,already ya fahimci maganan data kawosu,to amma yana da wani irin nutsuwa da dattijantaka a jininsa,bazai hanasu magana ba,tunda ya riga ya gama yanke hukunci,baya tunanin kuma akwai abinda zai sauyashi. Da qyar ta tattara duk wani qwarin gwiwarta,ta sauke qanta qasa,da wannan tattausar muryartata dake da wani irin amo me sanyi akhnan din tace. "Barka da warhaka bappi". Kadan ya dubeta,cikin bagararwa kaman baiga wani canji tattare da ita ba yace. " Barkanki,kina lafiya?" Tambayar da yayi mata saita tsinkar mata da zuciya. Sultane yana nufin shi baiga komai tattare da ita ba?,baiga girman tashin hankalin data shiga ba?,baiga yadda nutsuwarta ke neman wargajewa ba?,baiga yadda komai nata ya sauya ba?. Bama wadannan ba duka,ita din da idan tazo agadez,duk wani motsinta na wunin ranar......duk yadda sultane yakai ga yin busy,duk yadda itama takai ga shigewa wasu hidimomin.....koda sau daya ne a qalla a kowacce rana sai taxo sunci abinci tare,walau na safe ko na dare?,wasu lokutan ma idan ya samu sukunin ayyuka da kyau sukanci na rana ne tare. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Tana zama ta sake sosai dashi fiye da yadda take sakewa da kowa,wani lokaci fiye ma da yadda zata sake da mammina.....sama da yadda zatayi hira da ita. Ya bata duk lokacinsa,ya saurareta,ya kuma bata shawarwari. Wasu shawarwarin sun shafi rayuwarta ne,wasu sun shafi sahel couture,wasu kuma fadakarwa ne da jan hankali dangane da rayuwa,amma yau duka sultane ya ruguza wadannan abubuwan don kawai yana so tayi aure?. Yafi kowa sanin auren nan ba wajibi bane......bai zama wajibi a kanta ba,amma ya matsanta ya daga hankalinsa,to ko sultane ya fara gajiya da ita ne?. Ta tambayi kanta da kanta,bata kuma kai ga lalubo amsar ba muryar mammina ta sauka a kunnenta. "Ranka ya dade.......alfarma mukazo nema" Ta fada tana sake qanqan da kai. Kansa ya daga a nutse ya kalli mammina. "Allah yasa zancan bame tsaho bane,don ina da baqo me muhimmanci da na gayyata zamuci abincin dare dashi" Ya qarasa maganan yana kallon katafaren agogon dake tsaye da qafafunsa wanda akayi da wani irin qarfe daya bada shape na gidan sarauta. Wani irin bambarakwai sukaji maganar ta saukar musu,girman maganar a kunnuwansu ya sanya suka kalli juna a sanda idanun sultane yake kan agogon,kafin ya janyeshi a hankali ya maida dubansa kan mammina din. "Wacce alfarma ce?,Allah yasa batafi qarfina ba......bata kuma shallake iyakoki na ba" Ya fada hankali kwance,yana barin kwanyar akhnan dama ta mammina da lisaafin wanne irin baqo ne haka me tsananin muhimmanci a gurin sultane?,har yana batun su gaggauta fadin buqatarsu don lokacinsa na baqonsa ne kenan?. Wani abu akhnan taji ya tsaye mata a wuya. A iya saninta,ita kadai ce,ita daya ce keda tarin wannan muhimmancin a gurin sultane,to amma waye haka ya samu nasara ya shammaceta,yake kuma neman daidaito kan matsayinta da ita kadai ta cancanci ta sameshi?. Wani abu me qarfi mammina ta hadiye tana qoqarin saisaita muryarta,tare da bad da tunanin dake neman yin wasa da kalaman data tanada saboda lokaci irin wannan. "Ba wata buqata da zatafi qarfinka Allah ya baka yawan rai......komai yana biyayya ne ga umarninka......haka nan jin qanka......ya ta'allaqa ne akan kowa,ballantana kuma kan iyalinka da kuma shalelenka" Takai qarshen maganan tana nuni da akhnan dake zaune bata ko qwaqwaqwaran motsi. "Karki damu da dukka wadannan bayanan,jeki kai tsaye ga bayananki" Ya fadi yana qara nesanta fuskarsa da dukkan wata fara'a. "Me martaba......muna neman kayi mana rai.....kayi mana alfarma,ka janye zancan hakeem daga kanmu.......ka dubi......." "Zaituna" Kiran da sultane yayi mata kenan,wanda ya sanya gabanta wani muguwar faduwa. Sautin daya kirata dashi,da kuma kiran da yayi mata kai tsaye ba sakayawa ya tabbatar mata cewa.....lamarin yayi wani irin zama cikin zuciyarsa......hukuncin ya samu dukkan tabbatuwar da babu alamun janyewa. "Zaituna......daga yau daga kuma yanxu.......inaso ki janye kanki daga cikin wannan batun.....bama ke ba,inason duk wani wanda yakeson ya tsira daga fushina ya cire hannunsa.....wannan din hukuncina ne......wannan din zartarwa tace da babu wani abu da zai canzashi. A wannan shekarar,zan aurar da diyata ga wanda na gamsu na kuma nutsu da addininsa tarbiyyarsa da nasabarsa,zan aurar da diyata kamar yadda musulinci ya baawa uba daman zabawa diyarsa budurwa miji......saidai idan zata nuna masa iyakarsa ne.......zan aurar da khadeeja kamar yadda kuma musulunci ya tsara......ba shawara nake nema ba bare a kawomin mabanbantan ra'ayi". Ya fadi da wani irin yanayi dake nuna babu sassauci ko canzawa a maganarsa. Wani irin kalar tashin hankali ta dinga ji yana sauko mata. Ba abinda ke gilmawa a idanunta a sannan sai gata an daura mata igiyar auren HAKEEM. Gata a qarqashin inuwar bagidajen mutum irin hakeem din,tana karba daga umarninsa,tana kuma gaza yin komai da haninsa. Wani abu ya harba cikin kanta,taji kamar an samu allura ne an soka mata. Taji wani energy a jikinta da yake bata cewa......tayi dukkan me yuwuwa wajen nunawa sultane batason auren HAKEEM,tayi dukkan abinda zatayi don tabbatarwa da sultane qudurinta da kuma ra'ayinta,ba tare da jiran shawara ta biyu ba ta miqe. Kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki kai tsaye ta zarce tana takawa zuwa inda sultane yake zaune. Da mammina da sultane din binta sukayi gaba dayansu da kallo,ta qarasa,sai ta sulale a hankali tana zubewa a gabansa kaman me neman gafara. Ta sadda kanta qasa,zuciyarta na tsananin bugawa da yadda taga sultane ya zube mata dukka idanunsa. Wasu zafafan hawaye ne suka subuce mata a sanda bata shiryawa zubarsu ba,kawai sai taji bata da wani sauran jarumtar boyesu ko hanasu zuba. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 76 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX _________________________ *SHEIK HAISAM* ★★Wani sashe ne na musamman cikin gidan dashi kansa tsarinsa ya burgeshi. Na musamman din da zai sake tabbatar maka da hakan saboda kalar masu tsaron dake kowacce qofa da kusurwa da zai taka ya wuce. Babban abinda yake bashi mamaki shine,ta yadda kowacce qofa yazo zai wuce da hanzari suke janye masa ya ratsa ya wuce abinsa,wanda a binciken da yayi iyalin sarki ne kadai.ko 'ya'yan cikinsa ko wanda yake da mugun kusanci dashi ya isa ya ratsa wadannan qofofin kansa tsaye,va tare da wata zazzafar tuhuma ba,har kuma ya tsinci kansa kyakyawar harabar da yake takawa a yanxu,wanda tafi zubu da makadeden tsakar gida na alfarma,wanda daga nan yake iya hango kyakyawar balcony din dake lullube da shuke shuke,balcony din da ita zata sadaka kai tsaye da qofar makadeden parlor din me martaba. Guri ne da muddin ka iskoshi baka buqatar iso game martaba,dukka shingen daka tsallaka ka wuce suka baka daman isowa ga nan din sun gama tantanceka,don haka kai tsaye ya dinga takawa yana nufar balcony din. Sanye yake da wata jubah me sulbi kalan gray color kalar data haska ta kuma fidda tsananin kyan fatarsa na asalin qabilar oromo me hasken kala data dara ta sauran asalin qabilar. Daga wuyan jubah jallabiyyar da hannuwanta wasu irin maballai ne masu tsananin kyau da daukan hankali. Kansa kuwa hiram ne me kyau daya masa wani irin nadi da mafi yawan matasan larabawa 'yan birni keyi masa,shi ba yafashi yayi ba,amma yafi shigen kama da daurin dankwali da aka saki jelarsa ta baya,wata kuma ya sauko da ita kafadar hagunsa. Tattausan unique scent dinnan nasa ke fita,iska tana kadashi gami da kwasarsa tana watsashi sassanni daban daban na sashen me martaba dama kewayensa,qamshin da yakan jimma manne a guri bar tafi ba,yakan dauki kwana uku ma musamman idan har haisam ya zauna a gurin ne na wasu awanni. Qafarsa wani lafiyayyen farin takalmin fata ne,wanda ya dace da torches din jikin amama din kanshi(hirami) da kalarsa ta kasance gray da torches na white. Koda sau daya ka aza idanu a kansa lallai zai burgeka,komai nasa yana nuna tsantsar ilimin addini daya cakuda da wayewa ta fannin sanin duniya da abinda ke cikinta. Wata irin wayayyar siffa ce dake kwance cikin duk wani motsinsa,wadda ta cakuda da tasirin addini da wani iri kamala da kwarjini da alqur'ani yake zubawa dan adam. Can qasan maqoshinsa yayi bismillah a sanda yake dora qafarsa saman step din farki na balcony din,bismillah din da adams apple dinsa ne kawai ya motsa,wanda ya fito sosai daga saman maqoshinsa kaman idan ka sanya hannu zaka iya ciroshi. Manyan idanun nan nashi da shigowar dare ya sanya suka rusuna kadan ya ware a hankali,yana duban mutumin da baya iya ganin fuskarsa sai faffadan bayansa,yana maqale sosai da wani irin salon tsaiwa jikin tafkeken window din dake kai iskar tsirrai me sanyi dake busawa a gurin zuwa cikin ainihin parlor din. Kaman yadda ci gaba da takawan da yakeyi bai hanashi ci gaba da kallon bayan mutumin ba......wanda da ganinsa basai an gaya maka ba qaqqarfa ne......hakanan takunsa bai dauke hankalinsa ko na mutumin daga tsaiwar da yakeyi ba. Qasan takalminsa yana da laushi kaman yadda saman takalmin keda laushi,wannan ya sanya hankalinsa ya gaza daukowa don da alama bayajin kowanne irin sauti,sai sake maqalewa da yakeyi jikin window din sosai,da alama akwai abinda yake tsananin buqatar yaji,abun kuma daya kasance me muhimmanci qwarai da gaske a tare dashi. Sannu a hankali mamaki ya soma wanzuwa qasan zuciyar haisam,ya kuma katse duk wani nazari da yakewa katangun dake kewaye da sassan sultane din ya maidashi kacokam kan mutumin. Wani zuzzurfan kallo ya masa guda daya daya dasa masa wani qaqqarfan zargi me girma a zuciyarsa game da mutumin da ko fuskarsa bai samu daman gani ba,bai kuma yarda yayi wani motsin da zai alamta masa tahowarsa ba,har sai daya isa saitin qofar parlor din,ya soma zame takalmin qafarsa ta hanyar yin amfani da dunduniyar daya qafar sannan ya saki wata taqaitacciyar gyaran murya mara amon sauti idanunsa kafe akan mutumin. "Waaqa!(god!)" Ya fadi a razane sanda yake waiwayowa da hanzari cike da mamakin wanzuwar wani dan adam a gurin bayanshi. "OROMIA?" Haisam ya furta can qasan ransa cike da zallar mamakin jin fitar yaren oromo daga bakin mutumin,mamakin da ya gaza boyuwa ya wanzu saman fuskarsa dama idanunsa,ya kuma kafe TAMIM da kallo duk da a lokacin bai kamata cikin tsarin aikinsa yayi hakan ba. Idanunsa ya maida ga goshin tamim dake tsatstsafar da zufa,abinda ya sanya tamim wanda shima ya zubawa haisam idanu kai hannunsa ga goshinsa,ya kuma shafo gumin yana dubansa hannunsa. Idanunsa ya sake maidawa kan fuskar haisam,zuciyarsa cike da wani irin madaukakin mamaki da kuma tarin tambayoyin "Waye wannan?......waye shi?,yaushe ya wanzu cikin masarautar agadez?,a wanne lokaci ya samu matsayi irin wannan?,matsayin ketawa ta sassan sultane kanshi tsaye?. Ba dan rakiya?,ba iso?,ba tsarewa daga gurin masu tsaron sassan?. So yake yaci gaba da kallon idanun haisam ko zai iya karanta ko sansano wani abu tattare dashi,amma wani irin kaifi da kwarjini dake fita daga idanun haisam din sun danne nashi. Kasa jurar ci gaba da kallon fararen manyan idanun haisam din yayi,sai ya janye nasa,yana maidasu wani sashen cikin Tsananin mamakin jin wani baqon abu tattare dashi. A hankali haisam ya janye dubansa daga kan tamim din,ya tura sliding door din falon,abinda ya sanya tamim samun daman waiwayawa yana kallon haisam din a sanda ya fara takawa yana barin farfajiyar cikin jin wannan nauyin yana zartawa yana son murqushe zuciyarsa da duk wani karsashi nasa. Tashi guda kuma yana jin wani irin nauyi da wani abu me kama da tsoro yana son lullubeshi. "Bappi....." Akhnan ta kira sunan sultane din da wani irin rauni daya cika muryarta,raunin da sultane din kadai ta yarda ya ganshi,raunin da bata taba yarda ta bayyanashi gaban kowa idan ba sultane din ko mammina ba. "Bappi.......kayi haquri,kayimin alfarma bappi,ka janye maganan nan,bazan iya auren hakeem ba......ka yafemin bappi na roqeka" Ta fadi da sanyin da sai daya daki zuciyar sultane din,saboda abune da ya jima shi kansa bai ganshi ba a tattare da ita,saidai kuma tunawa da yayi cewa wani gatan zai sake yiwa rayuwarta,sai ya gayyato wannan jarumtar tasa ya aza saman ranshi. Wani kallo ya aje mata me nauyi,kallon daya soma ratsa duk wani jini dake yawo a jikinta da wani irin sarewa da lamarin sultane,kallon daya bata tabbacin yin nasararta abune me matuqar wahalar gaske.....hasashen daya kusa tarwatsa mata kwanya saboda razani,tayi qasa da kanta cikin jiran tsammani,abinda ya sanya lullubin saman kanta ya hadu da sassalkar sumar nan da tsananin kulawar da take samu ya maidata me sulbi,ya zame daga saman kanta zuw kafadunta. Saidai kafin shi ko akhnan wani a cikinsu ya sake cewa komai amon muryarsa ya gauraya a parlor din. Cikin muryar nan tasa dake da wani irin zurfi da kuma amo ya yi cikakkiyar sallamar dake nuna yasan haqqinta yasan kuma cikakken ladan da ma'abota cika sallama suke samu. "Wa'alaikumussalam warahmatullah" Sultane ya maida martanin sallamar fuskarsa tana washewa da wata kwantacciyar fara'a,abinda ya d'arsa wani babban abu saman zuciyar mammina,tana kuma jin nauyin sautin muryar haisam har saman zuciyarta. Waye wannan daya samu nasarar gusar da fusata da bacin rai daga zuciyar sultane da sallamarsa kadai?. Kaman sultane yasan me take tattaunawa da zuciyarta,cikin nutsuwa da girmamawa yace. "Bismillah sheikh muhammad........kai da falon mahaifinka?". " Mahaifi?" Mammina ta maimaita kalmar can qasan zuciyarta,tana kuma jinjina girma da nauyinta. Wannan kalmar da wannan furucin na sultane ya sanya zuciyarta cikin zaquwa da son sanin waye wannan?,abinda yaja hankalinta kenan ta zubawa qofar shigowa idanu don ganin bayyanarsa. Cike da wannan cikakkiyar kamalar wadda ta cakuda da kaifin kwarjini da haibar jinin sarautar OROMIA dake jininsa ya sanya qafafunsa cikin parlor da cikakken nutsuwar nan tasa. Karon farko idanun mammina suka sauka a kansa,wata irin matsananciyar faduwar gaba ta saukar mata ba tare da tasan dalilinta ba. Dukka idanunta ta zuba masa sanda yake ketowa cikin gurin,tana jin wani irin yanayi da batasan wanne iri bane yana ratsa jikinta har zuwa cikin b'argonta a hankali,kamar wadda ake fifitawa iska tsakiyar sanyin hunturu. Kallonta ta maida kan sultane wanda ya miqe yana fadada fara'arshi. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Barka da zuwa sheikh......ga guri zauna na qarasa ganawa da me dakina" Ya fadi yana yiwa haisam din nuni da mazaunin dake daura dashi. Iska ta sake shaqa a karo na uku tana jin kamar kwanyarta ta fara birkicewa,kaman komai ya soma dagule mata,kai kaman hauka ne ma yakeson kama ta?,ko kuma depression ne yake mata sallama?. Banda haka ta yaya?.....ta yaya a irin wannan lokacin?,a daidai lokacin da take tsaka da gwabza yaqin neman sauko da sultane daga kujerar naqin da yahau,kuma sannan a lokacinne wai hancinta zai dinga dauko wannan ajiyayyen qamshin yana kawo mata kusada hancinta?.....shin da wanne zataji?,da qoqarin soke auren hakeem a kanta ko kuma case din wancan mutumin?. Mutumin da tun daga wancan ranar zuwa yau bata sake lafiyayyen bacci ba ita kadai?,mutumin da tun daga wancan ranar zuwa yau bata taba kwanciya ta tashi lafiya qalau ba tare da taga gilmawar wadannan idanun masu wani irin magnet cikin baccinta ba?,wannan idanun da take zargin ta sake ganinsu ko ganin irinsu a wancan ranar,a ranar data kawo kanta wajen sultane. Kamshin wani irin ajiyayyen abune da kwanyarta da zuciyarta ta yiwa mugun ajiyar da koda cikin baccinta zata shaqeshi ta tabbatar saita farka,komai nisa ko nauyin baccin,koda zata manta komai daya shafi wancan ranar,ba shakka ba zata taba manta wadannan abubuwan biyu ne WADANNAN IDANUN da kuma WANNAN QAMSHIN da har yanzu ta kasa samar da irinsa domin hujja. To ta yaya ma zata mance dasu?,bayan yana cikin manyan burikanta?. Bata da buri a yanzu days wuce zaqulo SHI. Wannan baqon da yaso tozartata ya tozarta nasararta da ajiyayyen tarihinta name tabbatacciyar nasara?. Muddin ta barshi ko ta haqura ko kuma ta manta ita din bata cika HALASTACCIYAR DIYAR SULTANE MUHAMMAD HAMMUD BA. Sam ko kusa ko alama bai lura da ita ba,har sai zuwa sanda ya tako da zummar zama inda sultane din yayi masa tayin zaman. Kanta yana qasa,abinda ya sanya wannan kyakkyawar sumar me kyau da daukan hankali bayyana sosai fiye da fuskarta. A hankali kuma cikin ba zata idanunsa sauka saman sumar tata,ya janye qwayoyin idon nasa da wani irin sauri yana canza direction dinsa zuwa wata shiyyar ta daban. Wani irin abune ya tsarga masa tun daga saman kansa zuwa tafin qafafunsa. "Subhanallah" Ya fadi can qasan maqoshinsa,adams apples dinsa suna yin sama da qasa duka lokaci daya. Gashin mace yana daya daga cikin al'aura a jikin mace,zai iya cewa tsahon girmansa bazaice ga randa yaga wani sashe na jikin mace haka ba,don hatta dasu Anani suna da doka a kansu kai tsaye daga gareshi,bai yarda dayin kowacce shiga da sukaga dama ba muddin ba'a cikin dakinsu bane,don haka zaiyi wuya ka samesu kansu a waje ko wani sashen jikinsu muddin ba'a dakinsu suke ba. "Bismillah muhammad.......nan dukka na gida ne,kaima kuma ka zama dan gida......ga mamarka nan zaituna........ga qanwarka kuma babbar diyata khadeeja akhnan". Sosai ta zuqi qamshin da qarshen harafin sunanta da sultane ya furta. Sake cika gurin da qamshin da yakeyi da kuma yadda wani ya samu darajar da zai shigo a sanda take ganawa da mahaifinta,har kuma sultane ya ajiye komai......ya tsaidata ya kuma tsaida uzurinta da hanzarinta,ya tsaya saurarensa da dukka girmamawarsa.......daga qarshe ya dinga hada dangantaka tsakaninta dashi,irin dangantakar ma ta YAYA da QANWARSA. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 77 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ____________________________ Dukka wadannan tunane tunanen suka harzuqata,ta daga fusatattun idanunta da taketa qoqarin controlling fushinta da bacin ranta da zummae saukewa koma waye wulaqantaccen kallon da zai sanya ya fahimci iya darajarsa,saidai kuma a sanda idanunta suka fada saman fuskarsa da take yau full opened......suka sauka kan wadannan kewayayyun idanun da suka shiga rayuwarta,suka kuma shiga dukka mafarkanta sukayi kane kane,sai dukkan komai ya kwance mata. Wani irin lallausan murmushi ya sakewa sultane daya qara masa haiba,ya canza gurin zaman daya tabbatar zai sake nesantashi da ganin wani sashe na surar gashinta,yana qoqarin maida idanunsa kan wayarsa dake hannunsa wadda tayi blinking har sau biyu,alamun shigowar saqonni a jere. "Allah yasa buqatata bata takura ka ba". Miskilin murmushin nan daya qarawa idanunsa wani irin sheqi ya saki,ya motsa labban nan nasa dake wani irin glowing su kadai,saika zargi ma ya shafa musu lip gloss ne. "Gayyata irin wannan girmamawa ce sultane........" "Bappi......zanfi son ka kirani da sunan,don sunan da diyoyina ke kirana dashi kenan" Ya qarasa fada yana maida dubansa kan akhnan. Da qyar ta jefa hannunta baya ta jawo mayafinta,cike da tsammani da kuma yaqinin haisam din zai maido dubansa kanta,saidai a maimakon hakan kai ya jinjinawa sultane kawai ya maida wadannan idanun mash kaifi da nauyi saman wayarsa yana qoqarin sanya ta a silent yana kuma furta "Barka da dare". "Barka kade yarona......ya qoqari?,Allah ya dafa ya saka da mafificin alkhairi" "Ameen ameen" Ya sake fadi cikin girmamawa. "Ammm.......mammina ga muhammad nan,sabon d'anmu,kuma malaminsu falaak dake daukansu darasi duk yammaci" Sultane ya fada yana duba mammina din. Wani irin numfashi ta fusgo,kafin kuma ta biya ta hado da aron murmushi daga wani loko can na zuciyarta,kafin kuma a nutse ta saci kallon yanayin zamansa da kuma saqar jubah din dake jikinsa,ta kuma dora da. "Barka da warhaka sheikh,muna maka maraba da shigowa cikin da'irar ahalin sultane,haqiqa lallai ka taki babbar sa'a da har ka samu matsayin D'A sukutum daga sultane.......kinga daga yau biftu kin samu dan uwa ko?". Murmushin farinciki sultane ya saki,yana jin haisam kamar da gaske d'ansa ne har cikin jininsa. Ido haisam din ya lumshe tare da budesu lokaci guda yana dan jinjina kai. Sautinta da yadda karin harshenta ke fita yake qoqarin harhadawa cikin kansa. Wani irin accent yakeji daga bakinta daban,accent din da yake ji daga bakinta kamar ya banbanta da sauran harsuna da yaji sunyi magana cikin agadez. Idanunsa ya daga a hankali ya sauke kan mammina,wani kallo qwaya daya amma da aka yishi da tarin manufofin dake dauke da harsashe me zurfi. Idanunta ta lumshe tana qoqarin daidaita wancan qamshin a hippodrome......wannan qamshin a ranar da ya saketa ta kusa faduwa kusa da dakin hutawar sultane......da kuma wannan lokacin a yanzu da qamshin ya mamaye ko ina da wani irin yanayi da taji yana harbawa har saman kanta yana kuna sake dawo mata da ranarsu ta hippodrome data yiwa laqabi da BAQAR RANA. Ranar da har ta koma ga mahaliccinta bata jin zata bace a kwanyarta. A nutse mammina taci gaba da satar kallonsa qasa qasa,kowanne abu a jikinta daka iya bata signal akan komai yana motsa mata gami da ajiye mata wasu baqin yanayi a jikinta. Ba tambayar dake neman dakusar da nutsuwarta irin son sanin WAYE SHI?. Duk da cewa kunnuwanta sun jiye mata kuma kwanyarta ta ajiye mata batun MALAMINSU FALAAK ne. Sai takejin kamar sultane na zolayarsu ne......sai takejin kamar sultane na son tsokanarsu ko gwada hankalinsu ne. Ta aminta zai iya zama malaminne,saboda wani irin haske da ajiyayyen kwarjini da take hanga tattare dashi,amma ko da malaminne bawai malaminsu falaak ba,yafi kama da qasaitaccen malamin da gata da hutu suka huda jikinsa. Yaushe ma ya shigo masarautar amma bata samu labari ba?,yaushe ya soma rayuwa cikin ta ita bata taba sani ba?......hakan yana nufin tayi sakaci kenan?,hakan yana nuna akwai sauran qofofi data bari a bude wanda bata toshesu ta hanyar zuba masu bata masaniya ta wannan qofar ba. "Akwai sauran gyaran daya ragemin" Ta fadawa kanta,tana jin bata da sukuni har sai tasan wayeshi. A tsarinta cikin lokaci me muhimmanci da tsada cikin rayuwarta irin wannan,bata buqatar baqon abu cikin masarautar agadez,mace ko namiji,yaro ko babba,don dukkan wani wanda yake rayuwa cikin masarautar tana da dukkan wani bayanansa,na rayuwa hali dabi'u yanayin aiki da sauransu,samun qarin wasu baqin zai zame mata kamar maida hannun agogonga baya ne. Nutsuwa ko sau daya bata kusanceta ba,ta kwantar da wadannan idanun nata sosai tana qoqarin karantarsa a duk wani motsi nasa,cikin salon da ba kowa bane zai karanci haka kai tsaye. Saidai kuma cikin jikinsa yake jin akwai wani unusual kallo dake fita daga wani bangaren na dakin zuwa jikinsa. Bai motsa ba amma jikinsa ya gaya masa haka,yaci gaba da qoqarin maidawa beeno saqon gaggawa daya tura masa,yayin da wani sashen na kwanyarsa yaci gaba da aikin saita daga wanne sashe wannan kallon yake fitowa ba tare kuma daya daga kanshi ba ko sau daya. Agogo sultane ya kalla sannan ya maida dubansa ga akhnan,cikin sautin nan nasa dake cike da nutsuwa da kamala yace. "Ina saurarenki.....mene kike cewa kafin yanzu?". Maganar ba iya akhnan kawai ta daka ba,harda mammina. Ta dauka tunda baqo ya iso gurin,baquwar fuskar da babu ita cikin masarautar maganan ya wuce. Blue eyes dinnan nata da sukayi wani irin jirkicewa ta daga ta kalli fuskar sultane,sai kuma ta maida kanta qasa ba tare data iya sake cewa komai ba. Ta yaya zata bari rauninta ya bayyana a idanun wani bare?,barenma da take qarfafa zargi me girman gaske a kansa.....wanda muddin wannan zargin nata ya tabbata,tayi rantsuwa da ubangijin sammai da qassai saita tozartashi mafi munin tozartarwa. ((Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Duk da wani sashe na zuciyarta yana mata tantamar haka. Ba wani kidahumin malami irin haka,da bai gama sanin kansa bama ballantana dabbobi ya iya sarrafa dawakai haka......ya iya hawa doki da dukkan qarfin izza da qwarewa irin haka,zuciyarta tana cika da tantama idan ta tuna wannan.....babu wani malamin addini dake da wannan zarrar,ba wani kidahumin malami da xai iya tunkararta har ya iya hada tsere da ita. Ko waye wanda yayi hakan,tana da imanin cewa akwai tsartuwar jinin jarumta a jikinsa. Akwai wani yarfi na izza tattare cikin jininsa,akwai kuma wani abu na daban ma tattare dashi da kaifin idanunsa suka kasa barinta a mafarkai mabanbanta. Taga maza masu tarin yawan adadi a rayuwarta......masu tsananin zallar madarar kyau daga mabanbantan qabilu,cikinsu harda mazan qabilarta da sukayi fice a fanni na kyau a qasarta dama dukkan qasashen africa dama duniya gaba daya......mazan da suka yarda su sadaukar da komai nasu don ta aminta ta zama mallakinsu,amma babu wani namiji qwaya daya da wani abu nasa ya tsaye mata a rai,kuma wai har ya zama abokin mafarkanta sai a kansa. A hankali cikin kuma hikima ta daga idonta ta aza akan haisam. Sam sam kamar ma ba a gurin yake ba,kamar ma baisan wani abu dake wanzuwa a gurin ba,ya bawa wayarsa nutsuwarsa da kuma dukka hankalinsa. Abinda ya sake sanyata cikin mamaki,ba wani mutum da zaizo gaban sultane yayi haka,gayyata daga sultane ba qaramin alfarma bace,a niger kake ko a maqwabtan qasashen africa,amma shi gashi gaban sultane kuma yana danna waya?. Ko data daga kanta kuma ta dauka zata tsinciki alamun karkatuwar hankalinsa akan sultane ko shiyyar da akhnan take,amma ga tarin mamakinta,da dukka iya zurfin nazarinta bata hangi wata alama koda qarama ba dake nuna haisam yana tare dasu "Waye wannan?,wanne irin mutum ne shi?" Ta tambayi kanta da kanta,sai ta jinjina kan tana jin qarin wasu baqin dabi'u daban data hanga tattare dashi. Koda bataga alamun yana tare dasu ba,amma bataji yarda dashi ko kadan ba,ita din wata iri mutum ce da samun yarda daga gurin ta yake maka wahala,samun yarda daga gurinta yake daukarka dogon zango dogon lokaci da kuma dogon zamani. Sassauta murya tayi zuwa ga mafi qanqantar yanayi,yanayin da mammina keda yaqinin Haisam bazaiji ba tace. "Ranka ya dade......ina ganin wannan maganar bai kamata a yita ba a gaban baqo kuma bare......abune daya shafi iyali". Murmushin qasan rai haisam yayi,yana da wata irin baiwa ta kaifin ji matuqar gaske,kaifin jin da ya dinga bawa nanay tsoro. Ko yaya akayi magana,komai nisa muddin nisan yana kewaye da inda yake zai iya jinta. Daga idanunsa yayi ya kalleta,sannan a hankali yakai hannunsa ya riqo hannun haisam,sai a sannan din haisam ya daga kanshi yana duban sultane dake riqe da tsintsiyar hannunsa. "Nayi zaton daga yadda ya shigo ya riskemu zaki fahimci cewa daga yau SHI DIN D'ANA NE.....na dauka iya wannan zai gaya miki yana da girman matsayin da komai baza'a boye masa ba,na dauka kin karanci cewa ya zama DAYA DAGA CIKIN AHALINA.....komai na iyalina......komai na ahalina yana ciki,ba wani sauran abu da za'a boye masa". Girman bugunsu da maganan tayi ya sanya saida akhnan ta sake daga idanunta a karo na biyu ya saukesu kan haisam ba tare data shiryawa hakan ba. Ga mamakinta har a wannan lokacin sam bai dubi koda gefen inda take zaune ba,hakanan yanayin fuskarta bai nuna mata abinda take zaton gani ba. Farinciki murna da walwala take saka ran ganin kan fuskarsa,madaukakin farincikin da samun damar shigewa jikin me martaba haka ta farat daya,samun qazaitacciyar damar da ba wanda ya taba samun kwatankwacinta,tun daga sanda sultane ya zama magajin muhammad agga har zuwa yau din. Saidai a maimakon hakan,ba wani sauyi da yanayinsa ya nuna. Wannan fuskar me tarin kwarjini,wannan fuskar dake cike da wani irin kwantaccen kyau me daukan hankali.......wannan ran dake cike da wani izza ta sarauta cike yake da nutsuwar da zaka fahimta a karan kanka......hankalinsa sam sam baya tare da maganganunsu. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 78 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Wadannan idanun dai sune da suka sake haske saboda da hasken screen din wayarsa dake shiga ta ciki. "Zaiyi wahala ya kasance bashi bane wannan mutumin" Zuciyarta ta gaya mata kai tsaye ba kwana kwana,da kuma irin yanayin da indai ta d'arsa mata abu dashi to daga qarshe hakance take tabbata. Wani irin mahaukaciyar tsanarsa tayi gangamin gayya ta sauka saman zuciyarta,ta qanqance idanunta zuwa can ciki da wani irin kallo,tana fata koda sau daya ne ya kalli cikin idanunta ta soma ajiye masa saqon farko,amma hakan bata samu ba. Bata iya hadiye fushi ba,ba kuma kasafai ta fiya ajiye abu a ranta idan yana damunta ba,tana cikin jerin sahun mutanen da fadar abu yake zame musu sauqi da rangwame cikin rayuwarsu,hakanan nunawa a aikace ya zame musu dabi'an da bata canzawa. "To amma shi din ba kowa bane bappi.......bai rayu damu ba,baisan ya rayuwarmu take ciki ba.......hasalima ko cikakken magana da yaren abzinawa baya fita a bakinsa yadda ya kamata,ta yaya zai zama wani yanki daga ahalinmu?,waye shi?" Ta furta maganan Kai tsaye tana duban sultane. Sosai maganar akhnan ta yiwa mammina dadi,kamar ta shiga rai da zuciyarta taga kalar tambayar dake kai kawo a ranta,amma kuma tana takatsantsan da fitar tambayar daga ranta. Irin kallon da sultane ya ajewa akhnan ya tabbatarwa mammina inda ta yarda tambayar ta fita daga gareta ne data gama tozarta,gefe guda kuma zuciyarta ta cika fal da fargaba,kada sanadin wannan maganar tata ya kawo cikas gurin samun sauqin cikar muradinsu. Cikin wannan salon nata data saba amfani dashi tayi kiran sunan akhnan. "Biftu......kul dinki da jayayya ko qalubalantar hukuncin sultane,akwai wani abu da sultane zai yanke hukunci akai ace bai tabbata ba?". Wani murmushin ne daga qasan zuciyarsa da ba alamarsa saman fuska ko labbansa ya subuce masa,akwai wani boyyen sauti cikin lafuzzan matar,akwai boyayyen yanayi da ke bayyana wani abu da aketa qoqarin turashi nesa da zuciya nesa da mafitar magana saboda wani babban dalili na cimma quduri. "Wacece wannan?" Muryar omari ta ratsa kunnensa ta Bluetooth din kunnensa,cikin hikima ya dora yatsansa kan Bluetooth din daya saje da shape din kunnensa bata yadda zaka gani yadan latsashi,wanda daga wancan bangaren ya bawa omari sign na ya dakata kawai,sai ya gyada kansa a hankali yana sake matso da na'urar gabansa. "Da zaki qyaleta zaituna.....wataqila ta kawo wani abun da yafi nawa dacewa da muhimmanci..." Ya furta muryarsa na nuna alamun bacin rai,da kuma fara tunzura da yake dab dayi. Ta karanci wannan,bataso kuma komai ya kwabe,batason wannan raunin nasa da take qoqarin tayarwa ya koma ya kwanta,don haka ta miqa hannu ta matsa hannun akhnan data motsa da zummar yin magana,abinda ya faru cikin idanun haisam daya dan budesu cikin kallon qasan idanu da idan yana yinsa zaka tsammaci bacci yake. "Me yasa ta hanata ci gaba da magana?" Ya ajewa ranshi tambayar yana qoqarin janye idanunsa kan hannuwan nasu gudun wucewa iyakar kallon shari'a,saidai kuma kamar an fusgi kallon nasa sai ganinsa ya sauka kan tsintsiyar hannun mammina din. "Kayi mana afuwa.....kayi mana aikin gafara.....kada wannan abun ya zama silar kasa yi mata alfarma cikin alfarmar nan taka,cikin tausayin nan naka da jin qanka,don Allah.........muna fata ayi mana gafara" Ta fadi tana sadda kanta tare da sake matsa hannun akhnan a karo na biyu,kalaman da suka sauka kunnuwan haisam tare da dogon nazarin banguls din dake zagaye da tsintsiyar hannun mammina. Idanunsa ya janye a hankali cikin yanayin da ba zaka fahimta ba,daidai sanda ake sallama daga daga bakin qofar falon kuma aka daga labulen farko ana neman izini. Sautin muryar ya sake jan hankalinsa saboda jin wani sabon accent din kamar a yankin Ethiopia yake ba agadez ba. Kakkaurar muryar data masa kama sak da muryar mutumin da yaji a dazu. "Kana iya qarasowa" Maimartaba ya furta yana saisaita muryarsa. Cikin second daya ya bayyana cikin parlor,da shigar kayan sarki na yankin agadez......amma ba abinda haisam yake gani saman fuskarsa sai qasar Ethiopia a kalamansa,wanda sun bace bat daga kamanninsa babu ko qwara daya. A hankali ya aza hankalinsa a yanayin tafiyarsa,yana takawa ne da qwarin gwiwar da zata gaya maka wani ne a wajen sultane......da yanayin da zai gaya maka yana da girman matsayi da isa a gurinsa,sannna ya qaraso gabansa ya zube da yanayin da ya tunawa haisam ZAMAN GABAN SARAKUNAN QASAR ETHIOPIA. Wani irin zama ne da aka gaji yanayinsa daga manyan da tsofaffin qasar,yanayin zaman dake nuna zallar sadaukarwa......zallar bada kai.....zallar amanna da kuma biyayya. Idan har idanunsa sun nuna masa daidai,sai daya saci kallon akhnan kafin yakai hankalinsa ga sultane dake fadin. "Tamim sarkin aiki.......tamim gandun hidima" Wani kirari da yake bala'in farantawa tamim din rai,yana kuma sake bashi tabbacin cewa da gaske yakai wani qololuwar matsayi wajen sultane din. "Allah ya baka kyakkyawan qarshe,ya kula da dukka sha'aninka.....an kammala komai" Ya fada da tsantsar ladabin da ko idanunsa baya iya dagawa ya kalli sultane. "Amma tamim.......baka fahimtar muhimman lokuta da bai kamata ka dinga tsoma kanka a ciki ba?" Mammina ta furta da wata irin izza da qasaitar data hau kanta yanzu yanzu tana qure tamim din da wani irin kallo,gabanta kuma yana tsananta faduwa,wani irin bahaguwar bugun zuciya daga sanda tamim din ya bayyana,wanda batasan meye dalilinsa ba,amma tunda har hakan ta kasance take jin yaqini a zuciyarta AKWAI WANI ABU DA BA DAIDAI BA. "Tamim yana da matuqar qoqari zaituna,yana kuma da amanar da idan aka bashi aiki saiya tabbatar da gamsuwar wanda ya bashi aikin......ba laifi bane don yayi hakan......kaje tamim....zamu ganka in sha Allah" "Godiya nake Allah ya baka yawan rai.....ubangiji ya firgita maqiyanka". Ya fadi yana yunqurawa da zummar miqewa,daidai lokacin idanunsa ya sauka kan haisam,wanda har yanzu ga duk me idanun kallo idan ya dubeshi zaiga hankalinsa kacokam yana a kan wayarsa ne. Wani irin abu me qarfi yaji ya fusgeshi,zubawa haisam din idanu na wasu sakanni kafin ya janye dubansa a hankali yana takawa gami da ficewa daga shiyyar. "Inajin wannan maganar tazo qarshe......ni muhammad hammud na bayar da akhnan ga hakeem,watanni biyu kacal na bawa kowane bangare su gama shirinsu". Wani abu taji ya dunqule mata saman qirjinta,kamar yana shirin hanata shaqa da kuma fidda numfashi. *_BAYAN WASU SA'O'I_* Cikin qasaitaccen takunsa ya isa ga sassansa,wanda yana dab da dora hannunsa saman handle aka bude masa qofan. Abdii ne tsaye,yana dubansa da murmushi kan fuskarsa. "Welcomw captain obbo" Ya fadi da yanayin daya gayawa haisam a tsaye yaron hake tun dazu yana jiran dawowarsa. Da idanu kawai ya amsa masa,ya saka kai yana wucewa ciki abdii din ya take masa baya. Akwai maganganu da yawa a bakinsa da tambayoyi,amma yanayin obbo din ya nuna masa kaman akwai wata lafiyayyar gajiya a jikinsa. Mamaki kadan ya kamashi,mutumin da ya amsa gayyatan cin abinci,meye ya hadashi da gajiya kuma?. "Sai da safe zamuyi magana......i'm not cool now......karka sakani magana da yawa.....,ka kira salawi ka gaya masa yazo ya daukeni,qarfe sha daya na safe,kada ya wuce hakan." Ya qarasa fadin maganan yana tattakawa yan wucewa zuwa stairs din ba tare daya tsaya ba. Baki abdii ya saki kawai,shi yasa shifa yazo obbo ya barshi ya masa rakiya can cikin gidan,don ga ganewa kansa komai da komai. Saboda yasan halin 'yan miskilancin obbo din nasa, taba zama ya bashi labarin komai yadda yakeso ba,gashinan ma ko zama ya masa kyakkyawan kallo baiyi ba ya wuce sama abinsa. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Har ya juya,sai kuma ya laluba wayarsa dake aljihunsa da sauri. Sai yanzu ya tuna saqon da Menelik ta bashi ya isar dashi ga obbo din,sam ya manta,kuma a girmansa da mutuncinsa da take gani bai kamata ace bai isar da saqon a daren ba kamar yadda ya mata alqawari,don haka ya soma haurawa saman shima cike da tantama da d'ari d'arin kada haisam din yayi rejecting dinsa. Bawai gangar jikinsa bace ta gaji,a'ah,kwanyarsa dake cakude da tunani da hasashe iri daban daban ce ta saukar da gajiya ga kowacce gabarsa. Akwai abubuwa da yawa daya gani,wasu yayi hasashensu,wasu kuma jikinsa ya bashi. Cikin kowanne jini dake harbawa zuciyarsa yana sake samun tabbaci da yaqinin samuwar nasara.......yana ganin wani haske me girma kaman ya wulga cikin aikinsa,sai yakejin tamkar wata tafiya ce sukayi kuma sukazo bakin gaba. Bai shirya yin bacci da wuri ba,yana buqatar raba dare ya kammala dukka wani hasashe na kuma next plan dinsa as document kamar yadda ya saba cikin kowanne aiki,cikin kuma kowanne motsi. Yasa hannu ya zame amama din kanshi,take lallausan gashinsa me sulbi ya warware saman kanshi. Hannu yasa yana balle button din rigarsa,so yake ya zareta ya watsa ruwa me dumi da zai wartsakeshi daga duk yanayin da yakeji,sannan ya hada da zazzafan coffee dinnan daya zama jinin jikin duk wani d'a na asalin qasar Ethiopia. Yana balle button din hannunsa yaji an knocking qofar,da gajiyayyun idanunsa ya watsawa qofar kallo,bai kuma tsaya tambaya ba kawai ya taka ya murza lock ya budeta sannan ya jawota baya yana duban bakin qofar. Suna hada idanu da abdii din ya aza hannunsa saman tashi sumar yana shafata gami da fara sunne kai. "Dhiifama obbo". Da idanun nan nasa kadai ya tambayeshi dalilin knocking din,sai kawai ya fidda hannunsa a aljihunsa ya miqa masa wata fara qal din envelope. Duban takaddan yayi kafin ya maida duban nasa ga abdii,still da idanu ya sake tambaya ba tare da yayi magana ba. Har qashinsa yakejin girman kallo haisam irin wannan,da wannan body language din nasa me dafa mutum gwara ya buda husky voice dinsa ya maka magana. "Menelik ce obbo......don Allah karkayimin fada,alfarma tace nayi mata" Yayi maganan idanunsa suna nuna da gaske bayason ya masa fadan. Shuru yayi kaman bazaice komai ba,sai ya miqa masa hannunsa. Amamakance abdii yabi tattausan tafin hannun nasa da kallo sai kuma yayi saurin aza masa takardar ya juya yana boye dariyar farincikinsa. Da qafa ya maida qofar ya rufe,ya juya takardar sau biyu a hannunsa,sai ya qarasa ya jawo drawer ya zurata ya maida ya rufe. Sai da yayi hakanne ma ya tuna wancan saqon nata ma ko budashi baiyi ba. Idanunsa yadan lumshe yana budesu gami da kama jubah din nasa ya zare,lallausar vest dinsa fara qal ta bayyana,wadda ta tsumu da wannan qasaitaccen unique scents din nasa. Inda menelik zata fahimta......ba ita kadai bama,da sun samawa kansu sassauci. Bayason kowacce mace ta tsinci kanta a wahala ta sanadinsa. Baisan me zaiyi musu da zasu fahimci yana da sauran abubuwa da yawa a rayuwarsa.......ayyukansa masu muhimmanci da yinsu da kuma kammalasu yake jinsa ya zame masa tamkar Ibada,eh dole ne......don kubutar da rayuwar MOTII daga hatsari da barazanar da yake ciki tsahon shekaru ashirin da suka shude. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 78 __________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Wankan ya sakeyi da ruwan zafin,sannan ya fita parlor din dake manne da bedroom din ya hada coffee cikin mini coffee maker din da aka ajiye masa saman dan wani qasaitaccen table aka zuba duk wani kayan buqata na hadawa da kuma shan coffee. Sai daya sha cup daya sannan ya shimfida abun sallah. Wuturi daya rage masa yayi,ya zauna yayi tarin addu'o'insa sannan ya zame yana barin gurin. Sai daya daidaita tsakiyar gadon bayan ya ajiye abokin hirarsa wato coffee a gefe,ya rage hasken wutar dakin duka,ba hasken da kake gani saina system din dake gabansa. Cikin mintuna talatin ya kammala rubuta duk wani experience nashi na ranar,ya soke yatsunsa cikin na juna ya tallabi kumatunsa dasu ya zubawa rubutun idanu yana sake bibiyarsa. "Akwai wani baqon kallo da emotions a tattare da ita,akwai wani reflection dake nuna connection tsakaninta da wanda ka kira da TAMIM. Connection na tsananin jituwa ko kuma na akasin hakan.....yaya akayi wannan bawan dake tsaye bakin window sunansu yazo daya da wanda ya shigo parlor din sultane?......indai har ba amintaccen sultane ko wani daga cikin mutum ukun dake ciki ba......mammina......ita akhnan din da tamim na biyu daya shigo ba.....bata yadda za'ayi da tarin masu tsaron dukka qofofin ya samu isa wannan gurin dake da matuqar tsaro. Idan har kuma amintaccen ne na gaske,me ya hanashi qarasawa cikin kanshi tsaye?,me ya tsaya ji?,me ya tsaidashi cikin yanayin dake nuna zallar rashin gaskiya tattare dashi?. Gumin fuskarsa a sanda yaji motsinsa......kallon dake cikin idanuwan mammina sanda ta ganshi,me yasa bata qaunar baqo da zafi irin haka?,bayan masarauta ce.....cike take da tsari da yanayi na amsar baqi a kowanne lokaci,cikin kuma kowanne yanayi?,me yasa yanayinta yake nuna zallar kishi?,kishin kada kowa ya kusanci sultane?,kishin kada kowa ya fita kusanci dashi?. Yaga haka a idanunta sanda akhnan ke yunqurin yin magana da mahaifinta......kallon data masa yasha banban da wanda ta yiwa tamim ME YASA?. Me yasa take matsa hannuwan akhnan a sanda take yunqurin roqar mahaifinta?.....me yasa ta hanata magana?,me yasa bazata barta ba?. Siririn tsaki yaja,yana tuhumar zuciya da kwanyarsa. Wannan din ba abinda ya shafeshi bane,abinda ya shafeshi kadai shine yayi binciken dukkan wani dake da alaqa da sultane dama masarautar......ya kula da motsi da takun kuwa,ya kuma zaqulo wanda suke nema muddin yana a cikin masarautar yana kuma rayuwa. Amma baya ga haka,dukkan wani abu da zai faru.....dukkan wata alaqa ba huruminsa bane shigarta. "Tabbas akwai Oromian.......akwai Ethiopian cikin masarautar" Ya fadiwa kansa kai tsaye yana tuna lafazin mutumin daya fara gani a balcony. Yaren oromo ne fes saman harshensa......da accent din da sai haifaffen yaren kawai zai iya lanqwasa harshensa izuwa wannan yanayin. Idanunsa ya sake qanqancewa yana dawo da sautin muryoyinsu dukka cikin kansa. Akwai sautin mutum daya da harshen sa ya karye sosai.......ya kuma banbanta dana sauran mutum ukun dake wajen,lanqwasuwar harshen tasha banbam data saura. "Nasrumminallah" Ya furta yana motsa labbansa masu glowing dinnan a hankali. Idanunsa ya maida ya lumshe,yayi relaxing bayansa jikin kujera,dakin yayi shuru kamar yadda ilahirin gidan ya dauki shuru,yayi relax sosai kaman me sauraren wani abu,saidai kuma baya iya jin komai daga shurun da gidan ya dauka,sai qananun qwari dake bada mabanbancin sauti,da kuma qananun sautukan na'urori na Ac da sauransu da basuyi qarfin da zasu takura kowa ba. Nauyi idanunsa sukayi,kaman bacci yana son daukarsa,take duhuwar dake cikin idanunsa ta ingizo masa hotonta fes cikin gizanniya. "Subhanallahil azeem" Ya furta da sauri da wani qaramin amo da iyakarsa qasan maqoshinsa kadai. Zama yayi sosai saman sofa din,ya sanya yatsansa babba da dan manuni yana matse idanunsa,tamkar wanda hakan zai taimaka masa wajen fidda hotonta daya gilma masa a idanunsa. Ya dauki tsahon wasu mintunan a haka,sannna ya bude idanun nasa da suka kada suka sauya launi yanajin qirjinsa yana masa nauyi. Yana da wani yanayi da dabi'a dake saurin shiga kansa. A duk sanda yaga gilmawar wani abu daya shafi mace yakan zauna masa wani lokaci cikin kansa,wannan ya sanya yake cire kansa gami da nesanta kan nasa daga dukkan wani lamari daya shafesu. To amma a wannan karon besan me yasa abun keson dadewa cikin kansa ba tare daya barshi ba. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Ya fadi da cikakken nutsuwa yana qarasa kashe system din tasa,sai kawai ya dauki wayoyinsa ya zura bedroom slippers dinsa yana zarcewa dakin bacci. ★ *AKHNAN* Kayan jikinta kawai ta cire ta sauyasu da kayan bacci. Pyjamas masu rigar data tsaya iya cinya me dogon hannu,silk ne me dogon wando daya zauna mata,ya fidda shape din jikinta tamkar bawai kayan bacci bane a jikinta. Lamo kawai tayi saman gadonta,cikin jibgegen duvet dinta da tsabar laushinsa take sake nutsewa a dukka motsin da zatayi. Wani irin zafi zuciyarta keyi mata,a yau sultane yayi mata abinda bai taba yi mata ba,wanda ya soma jefa shakku a cikin ranta game dashi. Anya kuwa akwai wannan soyayyar?,akwai wannan qaunar?. Anya kuwa morsa safiyya bata shiga tsakiyar wannan alaqar ba?. Furuci da kuma tsaiwar da sultane yayi akan hukuncinsa ba tare da nuna alamun samun sassauci daga gareshi ba,wani abune daya bata matuqar mamaki. Wani abu ne kuma daya zo mata a bazata,don bata taba kawowa da tsammatar hakan daga gareshi ba. Saidai a jikinta take jin koma yaya ne ba zata taba yarda ta zama mallakin wani hakeem ba,koda kuwa hakan zai sababba fushin sultane ko kuma daukan mataki daga gareshi,wannan ya sanya take jin abun kamar baikai nisan da hankalinta zai tashi sosai ba,duk da hankalin nata ya gaza kwanciya yadda ya dace ace ya kwanta din,duk da alwashi da maganan da sukayi da mammina bayan fitowarsu na qarshe. "Kada ki damu ko kuma ki daga hankalinki,ni bazan gaji ba wajen nema maki da kuma sama miki farinciki da dukkan qarfina,da kuma dukkan iyawata muddin ina raye. Gobe ma zan koma,zan kebe da sultane,zan kuma tabbatar da cewa ban baro gurinsa ba saida labari me dadi". Wannan issue din ya kamata ace yafi damunta fiye da komai,amma saita tsinci zuciyarta tafi jin zafi da qunci kan abinda sultane yayi mata a gaban BAQUWAR FUSKAR da har yanzu take ji a jikinta bawai baquwa bace......tana ji a jikinta tasan fuskar......tasan kuma idanun. Maganganun da sultane ya fadi a kanta a gabansa ya dawo mata,qirjinta ya wani quntata guri daya,har a yanzu tana jin yadda ta wani muzanta,kaman a yanzu sultane keyi wadannan maganganun. "Idan ya kasance shine ne na hippodrome fa?" Zuciyarta ta jefa mata tambayar data tilasta mata ture bargon da take ciki,ta kuma miqe zumbur ta zauna saman tattausan gadon nata,kafin kuma ta janyo jikinta a hankali tana sauka daga saman gadon,tare da bin makunnin fitilar dakin ta sake kunnata. Ta yaya zata bari wani mutum qwaya daya ya gagareta a rayuwa?,abinda kaf cikin tarihin rayuwarta bata taba samun hakan ba?....ta yaya wani dan adam zai shigo qasar da mahaifinta ke mulki da ita ya dasa mata abubuwan da zasu tattare dukka nutsuwarta suyi gaba da ita?......ta yaya zata bari hakan ta kasance?,wanda kamar 'yar manuniya ce ta cewa ya raina girman izza da matsayin da take dashi,daidai da daga mata yatsa saitin idanunta. After dress dinta dake fidda sassanyan qamshinta daya kama duk wata sutura tata ta sanya,ta yane kanta da siririn mayafinta,ta murda qofar ta fito zuwa parlor din farko. Kai tsaye ta isa ga landline,ta kumayi kira zuwa dakin birra. Cike da mamaki birra ta daga kiran ta saka a kunnenta,bata kuma barta tace komai ba ta aza mata umarnin dalilin kiran. Ki dubomin tamim duk inda yake......ki kuma shaida masa ina buqatar ganinsa yanzu yanzu". "An gama" Ta fada a ladabce amma cike da tarin mamaki. Wayar ta mayar ta ajiye,saita sake takowa zuwa parlor na biyu. Duk girman gurin ba digon tsoro a tare da ita,kasancewar ta sani kewaye take da tsaron daba wani dan adam indai ba aljani ba daya isa ya iske inda take. Cikken motsi kawai mai qarfi ya isa ya kawo masu tsaron qofofinta zuwa inda take. Da wani irin yanayi take kaiwa tana kawowa cikin kebantaccen gurin data saba ganawa da tamim din. Cikin lokacin ba abinda take ji take kuma gani sai mugun dadewa da yalwa tayi,wadda ta aika ta kira mata tamim a duk inda yake. Duk da cewa a zahiri bawai dadewa yalwa tayi ba,to amma qaguwa da ganinsa a gabanta ya sanya take gani kamar jiran yayi tsaho da yawa. Wani irin zafi takeji a jikinta da zuciyarta gaba daya idan ta tuna cewa MATSALA zata iya kunno kai. Tana jin kamar akwai abinda yake ba daidai ba,akwai abinda yake buqatar ta sanshi ko ta gyara zamansa ya zamana a daidai. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Sallamar tamim ta sanyata Waiwayawa da sauri,bata kuma tsaya amsa sallamarsa ba tace. "Shigo.....qaraso ciki". Cikin sakanni ya bayyana,idanunsa cikin na mammina. Kanta ta jinjina a hankali tana hango wani abu cikin idanun tamim din. Ba haka ta saba ganin fuskarsa dama yanayinsa ba gaba daya,sai take hango kamar akwai wani abu daya taba ranshi. "Waye shi?" Ta jefawa tamim tambayar kai tsaye,kaman tana da tabbaci da masaniyar cikakken sanin tamim gareshi. Kai tamim ya jinjina,ya kuma matsa gefe yana neman gurin zama. Tun daga sanda ya baro gurin sultane bai samu zama ba ya shiga laluben wayeshi?. Ya sani tabbas zata buqaci sanin hakan,daga ganin irin kallon dake fitowa daga idanunta a kansa yasan hakan zata kasance. Haka kawai shima yaji wanzuwar matashin a gurin ya sauya yanayin gurin dana jikinsa ma gaba daya. Babban abinda ya fara fusgar hankalinsa shine.......kwarjinin da yaji ya masa,ya kuma cike gurin gaba daya duk da cewa a qalla zai bawa matashin shekaru kusan ashirin,amma sai yakejin wani irin girma nasa cikin idanunsa. Uwa uba......abu mafi girma shine wanzuwarsa cikin masarautar ba tare da shi ya sani ba. Babu wata halitta da zata wanzu cikin masarautar,ta yaro ko babba.....mace ko namiji saida saninsa,saida cikakken sani daga gareshi,sanin kuwa daya hada da inda ka fito,me zaka shigo yi?,adadin ikon da zaka iya samu cikin gidan,wa'adin zamanka dama fitarka dukka suna tafin hannunsa qarqashin tsananin qwarewarsa wajen aiwatar da dukkan wannan abun cikin hikimar da ba damqa masa alhakin hakan akayi ba,shi ya baiwa kansa wannan girman,shi ya baiwa kansa wannan matsayin. To amma dukka awannin daya shafe yana bincike a kansa abu guda ya samu. Malami ne da gaske,kuma dan cirani,maras wani gata ko galihu da yawan neman ilimi ya fado dashi hannun oustaz Ousmane,sukayi musanye a sanda oustaz din ya samu daman fita qaro karatu. Bashi da cikakken muhallin zama,don babu wanda yasan taqamaimen inda yake zaune,wannan ya sanya sultane bashi gidan da yake maqotaka dana gimbiya akhnan. Wadannan sune bayanan da tamim ya yiwa mammina. Ido ta zuba masa tana jin tantama akan bayanansa. Duk kuwa da cewa ta sani,batun qwarewarsa gurin iya bincike da kuma bin diddiqi akan komai bayyananne ne,yana daya daga cikin dabi'unsa da halayensa da take matuqar so take kuma alfahari a tattare dashi,to amma wannan binciken haka kawai takejin bai kwanta mata ba. Kanta ta dauke,tayi kuma taku uku zuwa gaba tana girgiza kanta a nutse "Bazan qaryata abinda ka binciko ba.....saidai wannan binciken ba shine ainihin abinda yake boye ba,inaji a jikina koda ba wani boyayyen al'amari a tattare dashi,to ba shakka akwai wani abu da zai iya faruwa a nan gaba,don haka inaso ka sanya ido a kanshi da dukka wani motsinsa,banaso ka bawa kowa wannan aikin,kai nakeso ka gudanar dashi da kanka,har zuwa lokacin da zan gamsu da cewa ba komai a tare dashi din........." Tayi maganan tana takawa zuwa ga hanyar da zata sadata da ciki,sai kuma ta tsaya cak. "Akwai alamun wani motsi daga K'ASATA?" Kai ya jijjiga. "Babu,ba wani motsi,komai ya tsaya cak,komai kuma ya lafa,al'amura suna ci gaba da gudana,a hankali sunansa da faruwar al'amarin yana bin awanni da shekaru yana salwancewa". Tsayawa tayi kaman me nazarin wani abu,murmushi kuma yana qwacewa daga kan fuskarta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 80 ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ____________________________ "Inajin kamar lokutan sa'ata suna dab da haduwa guri daya......anya ba zamu gwada wani abu ba?,.....idan muka dace sai ya zame mana hanya mafi sauqin da bamu taba zata ba,hanya mafi sauqin da muka jima muna jiranta shekara da shekaru" Zamewa kadan tamim yayi daga saman qafafunsa,yana jin zuwa yanzun ya kamata shima ya soma motsa nasa qudurin,quduri guda daya da yakejin dukkan wahala da bautar nan ta shekara da shekaru shine kadai zai wanke masa. "Ba laifi bane.....kuma a shirye nake na tsara hakan,a shirye kuma nake na tsara yadda komai kasance.......amma ina da wani shakku da kokwanto kadan" Ya fada fuskarsa da muryarsa suna suna muhimmancin abinda zai fada din. "Kamar?" Mammina ta tambayeshi tana riqe da labule. "Bazai zama matsala ko cikas ba?,bayan cikar ko kusa da cikar muradanmu idan na buqaci tukuicin farko daga gareki?". Ido ta zuba masa tana jin kamar ya raina girman izza da isarta,kamar ya raina dimbin arziqin da ta mallaka ita daya ranta. "Tamim........kana manta wace GIWA?,kana manta wace izzatu?,sunan GIWA kana taqaitashi ne kan ma'ana guda daya tal?". Murmushi yadan saki yana kada kai. "Wane mutum wane aikinsa.......ba daya da nake musantawa a ciki......girman tukuicin da zan buqata ne nake ganin kamar........" ".....kamar me?" Ta fadi cikin fara jin haushin maganganunsa. Qasa yayi da kansa cikin qasqantar da murya. "Allah ya huci zuciyarki ya baki yawan rai......tukuicin DAN MUTUM nakeso......shi zan buqata giwa,ban sani ba,a sanda na buqaci hakan zaki iya daukoshi daga hannu daga kuma mallakin ko waye ki maidashi mallakina?". Murmushi ya sake subuce mata,tana jin babu wani abu me sauqi sama da haka. Sanda yake gaya mata sai lokaci yayi.......sai lokaci yayi zai gaya mata tukuicin da yake buqata,wani lokaci takan jima zaune tana hasashe da tunanin me dame tamim zai iya cewa yanaso a matsayin sakamakon bauta na shekara da shekaru?.....amma a yanzun ta samu wani irin tarin sassauci data jima bata jishi ba. "Qarqashin mallakata akwai tarin jama'a......akwai tarin bayi nau'i nau'i,ka zabi dukka adadin dakaga dama,adadin da yayi maka.......zaka zama mutum mafi rabauta a duniya daga randa BURIKA BIYU na zaituna suka gama cika cif cif qarqashin jagorancinka,na maka alqawari zan baka duk abinda kake buqata". ★***Da kallo birra ke binsa sanda taga fitowarsa daga shiyyar mammina. Tadan sake kallon sararin sama tana qiyasce nisan dare a wannan lokacin. Ko ba'a gaya mata ba tasan cewa dare ya soma shiga sosai,kuma doka ce a dukka fadin gidan na haramtawa kowanne jinsi shiga sashen da bana jinsinsa ba,daga sanda akayi kiran sallar magariba. Abu mafi ban mamaki ya fito ne daga sassan da sukafi kowanne tsaro,sukafi kowanne dokoki tsaurara,kuma a cikin dare irin wannan?. "Gimbiya akhnan ce take kiranka" Ta fada tana rusunar da kanta ganin irin kallon da yake binta dashi,fuskar nan mai cike da qasumba a dinke tsaf. Sosai yaji batun yazo masa banbarakwai,saboda wannan shine karo na farko da ya soma jin hakan,sai kawai ya gyara damarar jikinsa da baya rabo da ita kulli yaumin yace. "Muje" Tayi gaba yana biye da ita a baya. Sanda suka isa a farfajiya ta barshi,ya soma bin gurin da kallo,don kuwa wannan shine karon farko da qafafunsa suka fara taka sassanta. Sassanta yafi kowanne sashe tsananin doka tsaro da kuma qa'idojin da SULTANE kadai aka yarjewa aga qafarsa a cikin gurin. Da idanunsa yake bin ginin da kallo da mamakin yadda aka tsarashi cike da tsaro da kuma ado da qawa. Zubewa tayi qasa tana shaida mata isowar tamim din,sai ta miqe tana gyara lullubin after dress dinta data rufe ko ina a jikinta tana fadin. "Muje". Da hanzari ya sauke kanshi daga nazarin da yakeyi yana maidawa inda ya jiyo takunsu,da sauri cikin tsananin girmamawa ya sauke kanshi,sannan ya karya gwiwarsa guda daya ya kaita qasa yayin daya cake tafin qafarsa a qasa da dayar qafar yana yin qasa da kanshi. Wani girma takeji yana ratsata a duk sanda yayi hakan a gareta. Yana cikin mutane da suke lissafinta na gaba gaba da sukafi kowa iyawa da sanin yadda zasu girmamata. "Tashi ka zauna" Tace masa bayan ta zauna,saiya tashi din amma ya tsugunna ne saman qafafuwansa. "Muhimmin aiki nake tafe dashi......kuma nakeso idan ka fara shi ba dawowa saida cikakken amsa da bayanai masu gamsarwa". "Umarninki kawai nake jira" Ya fadi kai tsaye,yana jin qarin samun wani matsayi daban yana tunkaroshi,yana jin cewa shi din me nasara ne da har gimbiya akhnan zata nnemeshi cikin dare irin wannan da buqatunta. "Basai na tsaya tambaya ko tantama ba......tabbas kana da labarin tseren dokina na qarshe a hippodrome da wani baqon mutum dan wata qasa?". Kansa ya gyada a hankali yana sadda kanshi qasa,sanin halaye da dabi'unta,da kuma dokar tsanar kallo da tayi a rayuwarta. Numfasawa tayi kadan ta kuma gyara zamanta,tana jin kamar komai zaizo da sauqi. "Ba wani abu me yawa kome girma nake buqata ba illa sanin wayeshi?,inason samu cikakken sunanshi da kuma qasar daya fito,kamanninsa da wani abu nashi daban da zai kaini zuwa ga inda yake.......sauran ni zan qarasa aikina da kaina". Murmushi ya saki kadan. "Aiki ne me sauqi qwarai wannan.......ki bani kwanaki bakwai kacal idan basuyi miki yawa ba" Kai ta jinjina. "Sun isheka?" "Tabbas" Ya fadi yana me bata tabbaci. Kai ta jinjina. "Yayi.......saidai akwai sharuda guda biyu cikin aikina,wanda idan ka kiyayesu nan gaba zaka iya samun damar da tafi wannan daga gurina". Wani irin dadi yaji yana ratsashi,wannan aikin aikine da zaiyishi koda babu ko sisi da zai rabauta dashi,aikine da yakejin zai iya kiyaye dukkan sharuddansa komai tsaurinsu.....wannan MATSAYIN da kusancin kawai yake buqata. "Na farko,banason kowa yasan da aikin nan.....na biyu kuma,inason ka gabatarmin da kowacce hujja shaida da kuma sakamakon bincike,ni zan fara dubawa da kaina.....ko idanunka ban lamunce suga komai ba" Ta fadi da dukkan yanayin da yake nuna da gaske take. Ta dauki wannan hukuncin ne saboda tanason zama ta farko da zataga waye din,idan har ya zamana wani wulaqantacce ne da darajarsa batakai tata ba,zai zamana babbana abun kunya wani ya san ta tsaya bata lokutanta masu tsada wajen yin tsere da wulaqantaccen mutum irinsa. Idan ita tafara gani,zatasan yadda zata lulluba komai ta kuma dauki matakin da zai gamsar da ita a sirrance. "An gama Allah ya qara miki daukaka" Ya fada yana dunqule hannunsa a qirji alamun dake nuna girmamawa da sallamawa. "Jeka.......zan sa ayi maka aike a safiyar gobe". "Godiya nake bisa wannan tarin girmamawa da karramawa da kikayimin na sakani cikin kebantattun al'amuranki" Ya fadi yana miqewa ya juya ya fice. Ajiyar zuciya ta sauke,tana wassafa irin yadda zata ladabtar da kuma hukunta mutumin. Ita daya tasan a ukun da zata sakashi,wanda saiya qare rayuwarsa yana dana sanin jaa da ita. ★★★Akwai wani sassanyan yanayi a tattare da ita wanda hatta da badee'a ta karanci hakan. Tana da hira wasu lokutan,duk da hirarta bata zama me tsaho da yawa,amma bata fiya zaman shuru ba musamman ga mutanen da sabo kadan ya shiga tsakaninsu irin ta da suke tare kusan mafi yawan awannin wuninta. Numfashi taja kadan,tana rufe shafin alqur'aninta. Ta juya agogon hannunta ta kalla sannan ta dora idanunta da sukayi wani irin laushi akan badee'a "Anya yau ma zaizo?". Dubanta badee'a tayi,yadda damuwa ke son yin tasiri cikin idanunta. " Ina kyautata zaton zaizo,a jiya da bazai zauna ba ya sanar......yauma inda bazai zauna din ba zai sanar,kaman yana cikin mutane masu tsari sosai da kuma girmama lokaci" Boyayyen numfashi ta sauke tana buda tafukan hannayenta. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) So take ta lalubo maqasudi kuma gurbin damuwar da takeji a ranta na rashin zuwansa karatu a jiya,yauma kuma kaman gashi hakan tana shirin faruwa,qarin mintuna ashirin,abinda bai taba yi ba tunda suka fara karatu. Ba zata iya tuna sanda ya qara mintuna biyar bama,yau kuma ga mintuna ashirin suna shirin salwanta. "Gashinan" Taji badee'a ta fada mata saitin kunnenta ta sigar rada. Wani matsanancin faduwa taji gabanta yayi,zuciyarta ta fara qara yawan bugunta. Tanason daga kai ta tabbatar,amma kuna tana tsoron wannan kwarjinin nasa. Gaza jurewa tayi,a hankali ta daga idanun nata da zummar koda a sace ne ta kalleshi,idanun nata suka sauka a kansa daidai sanda yake takowa cikin ginshira da qasaitar da baisan tana bayyana kanta da kanta a tattare dashi ba. A gajiye yake,irin gajiyar da hutu kawai yake buqata. Tun goma na safe ya fita,suka hadu da omari dasu beeno,har kuma qarfe uku suna tare suna duba abubuwa masu yawan da suka bawa kowa a cikin su tabbaci tare da yaqinin NASARAR AIKINSU tana rataye masarautar agadez,amma hakan baya nufin kuma su saki sauran masarautun da kowannensu ya saje da ita yana rayuwa a cikinta. So samu yayi zamansa cikin sassansa,ko gidansa dake waje,amma kuma bayason ko yaya yabar wata shaida ko digo ko wata alama komai qanqantarta da zata bar sahun zargi. Iya haduwarsu dasu a jiya kawai yana jin cewa dole ya sake matse kowanne motsi nasa. Indai abinda yake zargi akai ya tabbata to ya sani zai zama ana binciken bincike ne.......kallon kallo,idanu kan wasu idanun,wannan ya tilasta masa watsa ruwa me dumin gaske,sukayi jam'i shida abdii daya zube a nan saboda gajiya yana fadin bacci zaiyi,ya duba closet dinsa ya shirya cikin Moroccan jallabiyya maroon color da aka yiwa adon milk din zare. Hula dara ya dora saman kansa ja data dace da kalar rigar sak da sak,wannan ya sanya sassalkan gashinsa ya samu yadan fita kadan ta qasan hular,abinda ya qara masa wani irin ajiyayyen kyau da kuma kwarjini na musamman. Kusan yau duk inda ya gifta cikin gidan sai idanu sun bishi da kallo,kallon da baisan mafarinsa,tun daga cikin gida abdii ya soma,bakinsa ya lura taf yake da magana yanason kuma tankawa amma yayi masa birki,dole abdii ya hadiye yana satar kallon yadda kayan suka zauna masa,yaso ya bashi fuska ya fadi abinda idanunsa suka gani,amma rashin samun fuskar ya tilasta masa kama bakinsa. Taji wani irin kunya da nauyi sun saukar mata sanda idanunta suka fada cikin nashi. "Innalillahi" Ta fadi cikin jin kunya na hada idanu da sukayi,da yadda kyan da shigar yayi ta wafci idanunta da hankalinta,sai tayi qasa da idanunta tana maidashi saman qur'anin hannunta. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 81 ____________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ Shima idonsa ya dauke yana karantar wani abu tattare da yanayinta. Akwai abubuwa da yawa idan tayi da suke kasa kama da dabi'u da kuma yanayin saamee,abinda sam baya son tunawa ko hadawa kenan guri guda,don sam baya mata fatan ta fada yanayin da saame din ta fada. Ya karanci tasirin nutsuwa da kunya sosai tattare da ita,baisan me yake neman fusgar hankalinta ba?,tunanin daya sanya yaji zuciyarsa ta quntace guri daya,yana neman amsa da laluben dalilin da yasa irin hakan ke faruwa,duk da yadda yake yawan kaucewa duk wasu abubuwa,dukkan wasu dalilai da zasu sanya mace tayi falling a kansa. Wannan dalilin ya sanya me yawan daure fuska.......mara fara'a me fusataccen yanayi. Mutum me mugun nesa da dukkan al'amuran mata,don ya sani a yanzu bai shirya aure ba,dole ya kiyaye duk wani abu da zai sanya a shiga soyayyarshi. Yanaso yayi aure a sanda yake da cikakken lokacin kansa......don dausayin aljanna yake son ginawa......tattausar shimfidar soyayya qauna da rahama a cikin gidan sa kwatankwacin yadda annabi muhamamd S A W ya koyar. Bayaso yayi aure a sanda baida lokacin matar......bayason yayi auren da matar zata yita sadaukar masa.......zata yita haquri dashi da irin busy dinsa alhalin kuma ita tana cutuwa. Yanason yayi auren da MAWADDA da RAHAMA zasu zama shimfidar cikin gidan sa. Yanaso ya bawa matar da duk zata zama macen aurensa wani kebantaccen gata da zata sha banbam da kowacce mace a DUNIYA. Yana da tarin tsari da buri me yawa a gidan aurensa. Gidan SOYAYYA yakeson ya gina,ba gidan ZAMAN HAQURI ba. Kamar ko yaushe,tana jin yadda Aeera ke riqeshi da kyau tamkar taga mahaifinta,surutunta da bakinta cakwai tana iya jiyota. Abu daya dake sake zama ado a gareshi.....duk yadda Aaera takai ga zaqin surutunnan nata ba zaka taba jin nashi muryar ba. Wata irin cikakkiyar nutsuwa da kamalar zance gareshi,yana biye mata yana kuma amsa ta,amma sautinsa daga Aaera sai Aafreen dake kusa dashi sosai sukejin abinda yake fadi. Akwai ranar da badee'a ta matso saitin kunnen falaak da itama fiye da rabin hankalinta yana kansu,duk da littafi ne a hannunta a bude take dubawa. "Idan ina ganin mutumin nan,saina dinga raina ajin duk wata mace me aji.......jan ajinsa yayi yawa.......gaskiyarki fa uwar dakina,komai nasa cikin sarauta yakeyi......sai naga kamar mu ba mata bane,yadda namiji keda aji irin wannan,anya akwai macen da zata burge wannan?" Idanu qasa qasa falaak ta juya ta watsawa badee'a harara. "Dama ba karatu kike zama dauka ba?,yanayinsa kike karancewa?". Ta qarasa fada tana jin wani abu yana taba zuciyarta. Dan murmushi badee'a ta saki tana janye jikinta. "Afuwa nake bid'a,na tuba bazan qara ba,na gagara yin shuru ne wallahi". " Banason irin haka" "Ba za'a sake ba" Ta fada tana komawa ta zauna sosai. To amma sai maganar badee'a ta tsaya mata a rai. Maganganun badee'a suna shige da abinda ya jima yana kai kawo cikin ranta. Ta tashi gidan sarauta,cikakkiyar d'iyar gata gaba da baya,wadda ta mallaki dukkanin siffofin kyau da aji irin na cikakkiyar mace me tarin quruciya,cikin shekarun da duka duka suke sha shida zuwa sha bakwai. Tun a yanzun akwai masu kamun qafa da momma da kuma sultane a kanta,mutane masu yawan da batasan adadi ba,amma a duk sanda suka wanzu a muhalli daya ita dashi sai taji ta raina komai data mallaka. Kyan,quruciyar.....mulkin......sarautar dama ajin gaba daya. Ko a yanzun daya nutsu yana musu qarin qur'ani cikin muryar nan tasa dake shigen kama data sheikh afif muhammad taj,sai takejin a duniya ba wani sauti da yakai wannan dadi. A hankali ta zama aminiyar sauraron karatun qur'ani a yawan lokutanta na rayuwa,da kuma qira'ar sheikh afif din,kafin ta fara fitowa da wayarta tana recording karatun daya zame mata abokin fira. Abin yana yiwa momma dadi,nutsuwa ta sake shigar falaak din saboda abotar data qulla da sauraren qur'ani,tana sake samun tabbaci da yaqinin halayenta zasuyi kyau fiye da yadda take mafarki,domin shi qur'ani waraka ne daga dukkanin cututtukan jiki zuciya dama ruhi gaba daya. Ta dinga godewa Allah daya shigo da sheikh muhammad haisam cikin rayuwarsu a sanda take fafutukar inganta rayuwar 'yarta da jikokin da Allah ya azurtata dasu. Wani abu da falaak ta lura dashi shine,muryarsa tana qara daguwa ne da qara kaifi a duk sanda yake rera karatun qur'ani. Ta lura sautin yana kaiwa nesa kadan da inda suke,sai taji kaman komai na gurin ya sake nutsuwa ne da rerawar karatunsa cikin gwanancewa da hikimar sarrafa harshe dake kan harshensa dama wadda ke cikin littafin me tsarki. *_DAIDAI LOKACIN_* Da take zaune cikin balcony dinta,zama ne na jiran tsammani.......zama ne na jiran isowar mammina da ta shaida mata ta sake shiga gurin sultane a karo na biyu don karbo mata sassauci. Ta zabi ta kebe kanta a nan,ta kuma qona dukkan lokacinta ta jirayi mammina,don shine kawai abinda ya rage mata. A hankali sautin ya fara kai mata har inda take zaune,ya kuma fara shiga mata kunnuwa. Idonta ta lumshe sannan ta bude,sautin ya danyi nesa daga inda take jiyoshi,amma yana da wani irin kaifin tasiri daya soma sauka kai tsaye cikin zuciyarta. Inda ace inda take zaunen akwai hayaniya da ba yadda za'ayi ma ta iya jiyoshi. A hankali take bin kowanne harafi dake fita,tana kuma qoqarin zaqulo surar da ake karantawa,amma sai taji kwanyarta ta gaji gaba daya,ta kuma gaza gano komai. "Biftu" Muryar mammina ta haye saman sautin karatun,ta kuma fusgi hankalinta,saita waiwaya da sauri tana duban mammina dake tsaye. A hankali a sanyaye kuma ta miqe tana dubanta,jikinta ya bata,hakanan alamun rashin samun nasararsu ya bayyana saman fuskar mammina din. Hannuwanta ta sanya ta kamo mammina tana duban idanunta dake cike da tashin hankali. "Bai janye ba ko?" Ta tambayeta a sanyaye. A qa'ida yayi tayi maganan ya kamata taji tausayinta ko yaya,duk da cewa itama tana cikin tashin hankalin samun tasgaro kan hanyar data shareta fetal take kuma hangen babu wani sauran datti ko tsiro da yayi saura da zai bata matsala,sai gashi sultane yana neman zame mata BABBAN DALILIN DAMUWAR. Wannan tashin hankalin da take gani saman fuskar Akhnan shine garkuwarta......wannan tashin hankalin dake gauraye da fusata shine nata makamin guda d'aya daya rage.....amma hakan bazai hanata daidaita takunta ba,don haka ta kama dukka kafadunta ta maidata tana zaunar da ita. "Rashin samun nasara a kanshi yau ba shine yake nufin gobenmu ta saraya ba......idan bamu amintar dashi a yau ba gobe ko jibi tabbas zata sauya mana shi......amma dai....." Saita dakata sannan itama ta zauna tana fuskantarta. "Sultane ya kafe da irin nau'in kafiyar da ban tana ganinta a tattare dashi ba.....kici gaba da haquri,zanci gaba da qoqarina muddin mumfashina". Jijiyoyin kanta dana idanunta tuni suka motsa,ta kama hannun mammina din tana jin duk wata qwarin gwiwa da nasararta ta dogara a kanta. "Yayi abinda bai taba yi ba,bawai saboda rad'in kansa ba.....yayi ne saboda an sakashi,an dorashi a hanya an nuna masa.......bazan taba yafe mata b......" "Akhnan mana" Mammina ta kirata da yanayin dake nuna bata qaunar qarasa fadin abinda zata fadi din,yanayin da yasha banbam ainun da abinda ke qasan zuciyarta. "Ko ban fada ba a nan a gabanki.....zan fadi watarana.....watarana a gabanta,watarana a gaban kowa da kowa.....ta rusamin mafarkaina.......ta maida farincikina zuwa baqinciki na.....indai ni halastacciyar d'iya ce,kuma haifaffiya ga MUHAMMAD HAMMUD.....wannan zuciyar ba zata taba sonta ba". "Ba wannan keda muhimmanci a yanzu ba......abinda ya fishi muhimmanci shine ki.maida hankali wajen cikar burinki.......". Waiwayawa tayi bayanta,ta kuma qwalawa birra kira data tabbatar batayi nisa da gurin ba. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) "Ki tabbatar baki bar kowa ya shigo gurinta ba.......a barta ta zauna ta nutsu ita kadai,a samar mata da dukkan abinda zata buqata har sai zuciyarta tayi sanyi". " In sha Allah" Birra ta fadi a girmame,tana jin tsananin tausayin uwar gijiyar tata yana ratsata. A kwanakin tasan bata samun wani cikakken bacci,duk wasu yanayinta ba irin wanda ta sani bane a baya,ta juya tana bin bayan mammina don itama ta bata space sanda taga ta cusa yatsunta dukka goma cikin gashinta me santsi. Murmushi takeson ta saki na yadda hannu daya ke tafiya da yanayin daya dace,amma kuma har yanzu tana jin lokacin da zata saki murmushin bai qaraso ba. Agogon hannunta ta kalla sanda yalwa data bari a qofar farko take biye da ita. "Ki koma cikin gida.....anaso naci gaba da samun labari akan komai......idan nace komai ina nufin kowanne irin nau'in baqon motsi,babba ko qarami,banajin zan sake fitowa yau duka haraba,motsina da kai kawona a kwanakin nan yana yin yawa,yana kuma sauyawa daga yanayin da aka saba ganinsa a tare dani,banason zargi ko d'iso,wanzuwarsa a guri komai qanqantarsa MATSALA ce,ita kuma matsala kalma ce da mukayi hannun riga da ita". Kai yalwa ta jinjina. "Angama" Ta fadi tana juyawa gami da sauya hanya daga ainihin hanyar da suke kai. Su biyu suke takowa zuwa sassan nata,daga ita sai shehnaz din da bakinta ya kasa hutawa daga qorafin da mitar da takeyi tunda suka fito daga sassan nannie. "Duk yadda zaka yiwa nannie bayanin kafiya da taurin kan akhnan ba zata fahimta ba" Abinda aisa ta fada kenan bawai don hankalinta yana kan maganganun shehnaz da mitarta dari bisa dari ba,sai nisa da hankalinta yayi kan wani abu na daban. Tun daga waccan ranar da mammina ta gaya mata,ita zata bude office din akhnan,ta kuma ci gaba da tafi dashi hankalinta ya gaza gamsuwa da hakan. Tayita qoqarin ganin akhnan amma lockdown din data sanyawa kanta ya hanata faruwar hakan. Taje don ganinta sau babu adadi amma bata samu dama ba,ba kuma wai don batayi isar da zata karya tsarin akhnan ta shiga har inda take ba.....aah,tayi hakanne saboda kare aikinsu birra wadanda a sanda suke mata bayanin ta kafa musu sharadin kada subar kowa ya kusanci inda take tsoro ne fal idanunsu. Tsoron irin tashin hankalin da zasu fuskanta idan suka karya mata doka daya cikin tarin dokokinta. Tana respecting mutanen,don sun sadaukar da rayuwarsu da lokutansu gurin kula da buqatunsu,wannan ya sanya tabi umarni itama don kare musu aikinsu da mutuncinsu. Kwana daya tsakani kuma suka tafi diffa da nannie,sai dazu da azahar suka iso,ta kuma tarar da abubuwan da basa nan wasu a ciki suka kasance. "Mammina tace kada kowa ya shiga,a barta ta samu nutsuwa ita daya" Birra take sake shaidawa aisa a karo na biyu,tana jin nauyin girma irin na aisa amma a karo na biyu tana sake gaya mata ba zata samu ganin akhnan din ba,duk da tarin matsayi da kusanci da take tare dashi. "Wannan karon zan dan taba tsarin aikinki birra ki haquri......tana buqatar wani a kusa da ita" Aisa ta fada cikin qarfin gwiwa. Matsa mata birra kawai tayi,saboda ita a karan kanta tana ganin gaskiya a maganar aisa fiye da maganan mammina. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 82 ____________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX _____________________________ Me damuwa a rai ai wanda zai sassauta masa damuwar yake buqata,bawai a barshi da saqe saqen zuciya ba da ba'a da tabbacin me zata saqa masa. A hankali taji an sanya hannu an kuma zare hannuwanta dake cikin gashin kan nata,abinda ya sanyata daga kanta kenan tana sauke blue eyes dinnan dake cike da damuwa kan fuskar aisa dake gabanta da kuma shehnaz dake gefanta. Dukkaninsu su biyun saida jikinsu yayi sanyi,saboda wani irinn yanayi suke hanga tattare da akhnan din,wani irin yanayi da basu taba ganinsa tattare da ita ba. "Don me yasa zaki bawa damuwa dama ta nemi wargaza miki rayuwa?......me yasa zaki kashe wannan jarumtar juriyar da kuma dakiyar daga cikin jininki da jikinki?" Aisa ta fadi a tausashe. A yanzun dukkan abinda zai dawo da karsashin akhnan take nema,a yanzun abinda zai dawo da ita ainihin AKHNAN dinta take buqata,dukkan wasu dalilai da hanyoyi. Tana hango faduwar sahel couture haka kawai cikin mafarkanta,abinda zai iya zama babbar barazana ga akhnan din dama masarautar harma da yardar da sultane ya dauka ya basu. Bata zargin mammina ko daya da yin wani abu ba daidai ba,amma tana ji a ranta kamar mammina bata hangi abinda ita take hanga ba.....kamar mammina bata fahimci abinda takeso ta fahimta ba,wannan ya yanke mata hukuncin dole ta farfado da akhnan daga suman wucin gadin da tayi,wala'alla ta dauko matsalar daga inda ta dace da kyakkyawan gyara. Idanunta ta lumshe ta kuma ja numfashi me zurfi sannan ta fesar dashi ta bakinta. Batasan me yasa kwanyarta ke rikicewa ba......batasan me yasa take kasa gane kanta ba. "Mu koma ciki......akwai maganan da zamuyi" Aisa ta fadi kanta tsaye tana miqa hannu ta kama hannun akhnan din. Kai tsaye suka dinga ratsawa ta gurin,har suka bulla sassanta. Daya daga cikin parlor dinta suka dakata,dukkaninsu suna yiwa kansu mazauni. "Ki raba kanki da damuwa......tana iya ruguza kowanne kyakkyawan tanadi da ka yiwa kanka.....komai yana iya zuwa ya wuce a duniya,ba wani abu me tabbata" Kai ta girgiza tana duban aisa da wani irin yanayi,har cikin jikinta takeji ta gaji da wannan matsalar......wannan damuwar ta isheta haka. "Banda matsala irin wannan aisa......gobe na akeson ruguzawa......mafarkina da burina akeson wargazawa". "Don ance kawai kiyi aure akhnan?.....shin wai meye aibu ko matsalar hakeem?" Shehnaz ta fada mamaki yana kamata. Anya kuwa abinda zuciyarta ke raya mata na akwai wata matsala kebantacciya tattare da akhnan din ba haka bane kuwa?. Wani kallo akhnan ta ajjiyewa shehnaz. Akwai tarin banbance banbancen ra'ayi tsakaninta da su,bama su kadai ba.....tarin mata har yanzu bata hangi mace kamarta ba. Nata ra'ayin nata tsarin da nata rayuwar yasha banban dana kowacce mace,ba kuma zasu taba fahimtarta ba,kamar yadda itama ba zata taba fahimtarsu ba. Duk abinda ke zuciyar aisa ta dauki wani qatoton abu ta danne. Ta riga ta gama aminta ba wani fahimtar kalaman da zasuyi ita dasu,a yanzu matsalar sabgar saheel couture tafi buqatar a magance......ta shanshano ta kuma fahimci muddin akaci gaba da tafiya a haka,tabbas makauniyar tafiya kawai za'ayi wadda qarshenta zai kasance mafi munin abinda hankula da idanuwa zasu iya kalla. "Duba nan" Aisa ta fada tana zube mata takardu. Da idanu kawai ta bisu da kallo ba tare data sanya yatsarta ko daya ta taba kowacce ba,saita janye gajiyayyun idanun nata tana duban aisa dasu. "Ba abinda zan iya dubawa a ciki......me ya faru?". Shuru aisa tayi ta zuba mata idanu,bacin ran da mamaki yafi yawa a cikinsa yana zagayawa da ita. Yadda akhnan din tayi maganan tasan da gaske iya abinda yake ranta kenan,ita kuma tana buqatar ceton kamfani,dole ta motsa ta fara mata bayani. Tsahon mintuna akhnan tana kallonta,kafin aisa ta rufe da fadin. "Akwai barazana me yawa dake tunkarar kamfanin,akwai kusakurai da gyararraki cikin salon tafi dashi,wanda ba inda zai kaishi saiga durqushewa qarshe ya rushe gaba daya,akwai sabbin mutanen da suke buqatar horaswa da gwaji kafin zamansu saman kujerun da aka basu yanzu haka suna tafi dashi.......mammina tace na bude office dinki na shiga naci gaba da gudanar dashi......" "To me zai hana kiyi hakan?" Kai tsaye ta yanke hanzarin aisa din ta fada tana dubanta. Idanu aisa ta fidda. "Me zaisa nayi hakan?". Ido akhnan ta lumshe kadan "Mammina fa kika ce?.....ita ta hangi dacewar hakan,don me ba zaki aiwatar ba?". Kai aisa ke kadawa. " Aisa ba zata taba zama daidai da akhnan ba. Nazo miki da dukka bayanan nan ne don ki watsar da dukka wannan raunin da kika azawa kanki,ki tunasar da kanki akwai nauye nauyen wasu a kanki,ki karbi aikin da yake dama naki ne. Idan da akwai buqatar na karba naci gaba da jagoranci da babu gurbin zuwa miki da wadannan bayanan......shine your eyes biftu!" Aisa takai qarshen maganar da qarfin gwiwa da kuma wani emotion da yake tasowa daga qasan zuciyarta. Shuru ne ya ratsa parlor din,wuta tana daukewa kowa daga cikinsu. Saidai a shirun kowa da irin abinda yake kai kawo cikin ransa. Aisa.....shurunta yana da alaqa ne da jiran motsi daga akhnan ko ta maida martani ga maganganunta......yayin da shurun akhnan ya karkata ne zuwa ga sabon hayaniya me qarfi da take jiyowa daga can farfajiyar gidan. Hayaniyar ta mata kama da ire iren hayaniyar da kan motsa a gidan a duk sanda sultane yayi wasu muhimman baqi. Haka kawai taji qirjinta ya doka,wata irin fargaba tana saukar mata,fargabar data sakata miqewa a hankali tana dosar 'yar harabar dake maqalena falon wadda aka yita ta fuskar da zata iya ganin kusan duk abinda yake kai kawo cikin gidan. "Akhnan....." Aisa ta fada da zafi,sai shehnaz ta daga mata hannu,abinda ya sanya aisa dakatawa kenan,don tasan tabbas akwai dalilin daya sanya shehnaz din yin hakan. Suna a zaune suna hangen sanda ta fita farfajiyar tana kuma aza dubanta dukka ga inda take hangowar. ★Sake duban yalwa tayi da kyau da wani irin hautsinannen kallo. "Me kike cewa?" Ta maimaita tambayar yalwa,duk kuwa da cewa ta mata bayanin da koda baka fahimtar kowanne yare kana iya gane me yalwa ke fadi. Kasa yalwa tayi da kanta,ta sani wannnan labarin ba kalar labarin da uwar dakin nata zataso ji bane,amma kuma labari ne me matuqar daraja da tsadar da zai ya qara daga martabarta a idanunta. "Me martaba ne yake karbar baqi daga zinder.....wazirin qasar zinder,da shugaba limamai na zinder gaba daya wato mahaifin hakeem,wadanda sukazo da kayan neman auren gimbiya akhnan". Wannan karon ji tayi kaman ta koma ta zauna ko zata daina jin kamar ana hajijiya da ita,to amma kuma nuna rauninta a kowanne irin yanayi abune data jima da nesanta kanta dashi. Tana da tarin rauni,yana kuma bayyana,amma a muhallin da babu wani mahaluqi da zai gani,daga ita sai ita daya qwallin qwal,domin tana ganin nuna rauni gazawa ce da zata janyo maka raini gurin wadanda ke qarqashin sarrafawarka. "Ya akayi labari me girma irin wannan ya boyu har sai bayan ya tabbata?,labarin dani ya kamata na fara sanin da shi?" Ta yiwa yalwa tambayar. Kai yalwa ta jinjina. "Abun akwai daure kai,don ina tabbatar miki kaf! Fadin masarautar nan,ba wanda yasan da zuwansu......banqi ko morsa safiyya ba" Tayi maganan tana juya kai cikin alhini da jimami. "Morsa safiyya" Ta maimaita fadin sunanta kamar tana jinjina girman sunan. Kai ta jijjiga a hankali. Tunda har ya kasance sultane bai shaida mata ba.....tunda har sultane bai gaya mata ba bata zaton safiyya ma ta sani. Ita daya ce mutumin dake sanin boyayyun abubuwan sultane wanda ba wani mahaluqi da yasan dasu........ita kadai ce wadda yake shawarwarin da ba wanda yakeyi dasu. Koda batanan sukan zama ajiyayyun shawarwari har sai randa ta dawo ta fadi nata hangen akai. "Yaushe sultane ya fara koyon boye abubuwa?" Ta yiwa kanta tambayar da batasan ta fito sarari ba,har sai da taji yalwa tace. "Allah masani,amma dukkan alamu sun nuna akwai giftawar magauta a ciki". Dubanta ta maida ga yalwa. "Karbar gaisuwar sarkin zinder da mahaifin hakeem.....hakan na nuna tabbatuwar auren hakeem da akhnan?" Ta yiwa yalwa tambayar da ita kanta tasan amsarta EH ce. Sultane baya magana ya sauyata,bama sultane kadai ba.....dabi'a ce ta dukkan wani basarake data taba sani. Indai haka ya tabbata kenan akwai yuwuwar faruwar komai......akwai yiwuwar komai zai iya kasancewa......kasancewar da take nufin tarwatsewar abubuwa da dama. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Ginannen BURI.....ajiyayyar MANUFA......tsohuwar FANSA da aka jima ana mata tanadi. Kai ta jijjiga da wani irin qarfi. Koda komai zai jagule......koda za'a rasa rayuka da lafiya na wasu mutanen ba zata bari haka ya faru ba......akwai SADAUKARWAR LAFIYA da RAYUKA da zata faru cikin masarautar agadez kenan. RASHI zai faru,koke koke zasu yaiwata,har sai ta tabbatar komai ya tafi mata yadda takeso. Ba zata damu da koma waye ZAI SAMU ko ya rasa ba.....ba zata damu da koma waye ZAI QUNTATA ko ya shiga masifa ba....FANSARTA........BURIKANTA suna gaban komai. Ba zatace Allah ya taqaita ko ya sawwaqe ba......idan ya taqaita ko ya sawwaqe tana yiwa wadanda abun zai shafa BARKA DA MURNA. "Inason a yanzu basai wani lokaci ba,ki isar da saqon zuwan wadannan baqin ga kunnen akhnan" Ta bawa yalwa umarni. Tana kyautatawa kanta zaton samun mafita a zuwa da dawowar yalwa,tana jin motsin akhnan daga shi kadai zata tsago mafitar da zata bata haske a gaba. "An gama" Ta furta da sauri tana miqewa daga tsugunnon da tayi a gabanta. "TURQASHI!" Mammina ta fadi a sarari tana dunqule hannunta gami da kaiwa daya tafin hannun nata duka. "Ki nutsu......ki nutsu zaituna" Shine abinda zuciyarta ke maimaita mata,sai tabi shawarar zuciyartata,ta zuqo iske me yawan gaske tana aikawa hunhunta,sannna ta zauna a nutse saman kujerar tana qoqarin tattaro dukka kuzarinta da kuma kowacce qofa dake cikin qwaqwalwarta dake taimaka mata wajen bada tunani me kyau. Tana kallonsu amma tana son qaryata kanta.......tana duban sultane da baqinsa amma tana qaryata abinda zuciyarta take raya mata tattare dashi. Kayan sarauta na masarautar zinder......kayan hadimansu dama dukka wani yanayi irin nasu ba baqon abu bane tattare da ita. Dukkan baqon da sultane zaya fito da kansa ya tarbeshi ba shakka ba qaramin muhimmanci baqon yake dashi ba a wajensa. A hankali qafafunta da hannuwanta sukayi wani irin rauni sanda take hangen hakeem a cikinsu. Wata irin faduwar gaba ta daki qirjinta data sanyata dafe qarfen gurin da kyau. Kai ta girgiza a hankali tanason tankwabe kalar tunanin da zuciyarta ke kutso mata dashi. Daidai sanda taji birra na fadin. "Mammina ta aiko da saqo ta hannun jakadiya yalwa". Kai kawai ta iya gyadawa birra din,wanda ta kauce kadan,abinda ya bawa yalwa daman kutsa kai farfajiyar gurin. Tsam aisa ta miqe,tana jin hankalinta bai kwanta da tsaiwar akhnan a gurin ba. Uwa uba wanne saqone haka yalwa ke tafe dashi wanda yanayinta dukka ya nuna alamun a gaggauce take. Taku uku aisa tayi shehnaz itama ta miqe tabi bayanta. "Tace na gaya miki ki tattara hankalinki da nutsuwarki guri guda......baqi ne daga zinder wadanda ke dauke da dukiyar aurenki......a yaune kuma sultane zai basu tabbacin bada ke ga dansu bayarwa ta har abada da zata halasta aure a tsakaninki dashi". Kaman kunnuwanta basu jiye mata daidai ba haka taji,sai kuma ta soma jin kamar ana turata baya kafin ta dangane da jikin shehnaz da tayi tsaye a bayanta. Bata damu tasan waye ya riqeta ba,idanunta akan yalwa kamar itace sultane din. "Bayar da aure na?,karbar dukiyar aure na?.....ga hakeem din?" Ta fada da wani sanyi a muryarta,ba kuma kalar sanyin dake cikin zuciyarta kenan ba,don wata irin kalar wuta zuciyarta ke fiddawa da adadin zafinta da zuginta ya zame mata na daban.....kalar wanda bata taba tunanin rai da zuciya zasu iya d'an d'ana su kuma jure a rayuwarta bane. "Ba shakka.....haka abun yake". Da wani irin hanzari ta sanya dukka hannayenta biyu ta ture shehnaz dake riqe da ita,aisa tayi kan shehnaz da turwar tazo mata a bazata don kai mata dauki,gudun kada ta fada kan kujerar qarfen dake bayanta ta zame mata ciwo,wannan kuma shi ya baiwa akhnan daman ficewa daga farfajiyar da wani irin yanayi kamar name ficewar hayyaci. Da wata irin madaukakiyar murya me qarfin gaske take fadin. zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal* *Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank* *KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN* 09166221261 KO 08187255862 *Al'ummar qasar nijer 🇳🇪* *2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 500* *SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI* 09166221261 *GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE* *MTN CREDIT 700 ZUWA GA* 09166221261 *SHAIDAR BIYA* 09166221261 *_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_* *QASAITA👑* *HUGUMANKU CE*✍🏽 💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎 *H U G U M A* PAGE 83 ___________________________ *_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_* https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX ___________________________ "Wallahi bazan aureshi ba....zanje na sake jaddadawa sultane......bazan aureshi ba!.....bana sonshi!.....a rabu dani mana haka!" "Bita aisa......bita" Shehnaz da abun yazo mata a matuqar bazata da wani irin tarin mamaki ta fadi,sai aisa ta saketa ta kuma fita zuwa parlor din da sassarfa,inda dukka hadimanta sukayi tsaye cak cikin razana da tsoron fusataccen fushin da suke gani tattare da uwar gijiyar tasu. Tana dab da qofar farko,amma ba wanda ya isa ya kamota a cikin su,sai zallar tashin hankalin daya bayyana a idanunsu saboda maganganun da take fadi cikin bacin rai. Cafko hannunta aisa tayi,wadda ta qaraso gurin da gudu,sai akhnan din ta waiwayo tana dubanta gami da watsa mata wani irin kallo "Sakeni!" Ta fada a fusace. Duban tsakiyar idanunta aisa takeyi. Wannan fusatacciyar zuciyar data jima bata yunquro ba ayau ta ballo kenan. "Biftu?,baki da hankali?,a cikin hayyacinki kike?,sultane din zaki je ki tara gaban baqi ki gaya masa bakyason auren hakeem!" "Eh!......haka nake shirin aiwatarwa,don suma su sani bazan auri dansu ba.....banaso!....ki sakeni aisa!" Ta fada a tsawace da lallausar muryar nan da ayau ta zama wata me kaushi. "Bazan sakeki ba.....bazan kuma barki kije kiyi abinda xai zubda kimarki ba,ya zubda kimar masarauta,ya taba mutuncin sultane ba" Wani kallo me cike da tsananin bacin rai take jefawa aisa. "Idan ma baki sakeni ba naje.....bazan zauna baqinciki ya kasheni ba,zanyi abinda yafi haka.....guba zansha!.....guba zan sha na mutu kowa ya huta!.....naga wanda za'a yiwa auren ko?!" Akhnan din ta furta da madaukakiyar muryar da sautinta ya karade dukka falon da wajensa. Kasa cewa komai aisa tayi,sai idanu data zubawa akhnan a tsorace. Tasan fushinta.....wani irin fushine me girman tasiri da idan ya motsa tana yin kamar me aljanu,tanayin kamar ta rasa hankalinta ñe......amma na yau din kamar yana neman zarta hankali,yanxu qiyayyar aure a zuciyar akhnan har yakai haka?. Batasan sanda shehnaz ta iso guri ba,sai ganinta tayi ta rungume akhnan din ta baya kuka yana balle mata. "Ki daina irin haka biftu....meye haka?,kinsan girma da munin abinda kike fada?,da kanki kike cewa zakisha abinda zaki kashe kanki?......biftu ki dawo hayyacinki mana" Ta qarasa fada tana zagayowa gaban akhnan din gami da riqe dukka fuskarta cikin tafukan hannunta. Wasu irin hawaye ne suka cika blue eyes dinta da suke nuna koda wanne lokaci zasu gangaro,labbanta suka motsa,motsawar da aisa ta fahimci ta furta. "Astgafirullah ne" Wadda bata da sauti ko kadan. "Kowa ya wuce zuwa aikin gabansa" Aisa ta bawa duk wanda ke tsaye a parlor din umarni,yayin da yalwa ta qarasa korar kowa. Hannun shehnaz da akhnan din aisa ta kama da sauran dakakkiyar zuciyarta,ta kuma jasu kai tsaye zuwa daya daga cikin bedrooms din akhnan din suka shige ciki sannan ta maida qofar ta kulle ta kuma murza key. Tunda ta hango tahowar yalwa ta miqe tsam tana fuskantarta gami da jiran isowarta. Zubewa zatayi kaman yadda ta saba,saidai ayau hannu mammina ta saka ta riqe kafadar yalwa. "Me ya faru?" Ta mata tambayar da dukkan zaquwarta nason jin abinda ya biyo baya. Tamkar a gaban mammina din akayi komai haka yalwa ta tsara mata,sannan tayi qasa da kanta a yau din tana jin nauyi tsaiwa gaban mammina a maimakon durqushewa a gabanta suyi magana yadda ta saba. Kamar saukar ruwa da daukewarsa gurin ya dauki shuru,sai kuma sautin siririyar dariyar mammina ta ratsa gurin. "Zatasha guba?" Ta sake tambayar yalwa. Kai ta jinjina mata. "Qwarai haka tace". Kai ta kuma jinjinawa. "A gaban aqalla jama'ar da sukakai adadi nawa?". "Hadimanta da yawa.....ciki harda ranta ya dade aisa da shehnaz". Kai ta sake jinjinawa. "Hakan yayi kowa ya shiga lissafi.....ZATA SHA GUBA" Ta fadi kai tsaye tana sakin kafadar yalwa gami da yin taku uku baya don bada tazara tsakaninta da yalwa din. (Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862) Kai yalwa ta daga da sauri tana duban mammina din,abinda ya jawo hankalinta ta sake maida dubanta ga yalwa,da wannan murmushin da a idanu da yawa yake bayyana zallar kirkinta da karamcinta......saidai a wasu lokutan kebantattu,a wasu idanun a wasu yanayiyyikan yake zama baqin murmushi,kuma mafi munin murmushi. "Zata sha guba kamar yadda tace.....nayi laifi?,ita ta zabawa kanta ko?" Ta qarasa maganar tana duban yalwa. Da sauri yalwa ta girgiza kai "Ba shakka......zabinta kenan.....furucinta na qarshe kuma kenan". Dage dukka kafadunta biyu tayi tana takawa hankalinta kwance. " Tamim za'a nemo?" Yalwa ta fada tana duban bayan mammina. Maganan yalwar taja hankalinta,ta tsaya can na wasu mintuna kafin ta waiwayo tana dubanta. "Yaushe kika fara min hasashe da kutsa kai cikin wasu abubuwan da ba'a gayyaceki ko an nemi tajin ta bakinki ba?" Da hanzari tayi qasa da kanta,jikinta ya soma rawa a hankali,tana kuma tuna LAURATU a shekarun baya da suka shude......a shekarun daba ITACE AKAN WANNAN MATSAYIN BA LAURATU CE "Afuwa nake nema.....kaina bisa wuyana.......ayimin aikin gafara" Ta fadi tana hade hannayenta guri daya,hannayen da rawa kawai sukeyi. Ido sosai mammina ta zuba mata,tana karance da yanayin razanin data shiga. Iya wannan kawai ya gamsar da ita,saita juya a nutse ta fice ba tare data sake cewa yalwa komai ba. Wani irin razanannen numfashi ta saki bayan ta tabbatar da fitarta,ta koma ta zauna dab'as saman mazaunanta tana sauke wani irin numfashi dake gauraye da tsoro. Ba zata sake gangancin aikata abinda ta aikata a yanxun ba.....ba zatayi gangancin da abinda ya samu LAURE ya sameta ba,tanason LAFIYARTA tana son RAYUWARTA. *Tofa!!!!.....ME KARATU?.....shin kana hasashen abinda nake HASASHE KUWA?.....kana iya hangen abinda nake HANGE KUWA?.....TUNANINKA YANA KAIWA INDA NAWA YAKAI?* *SU WAYE ZASU MUTU?* *WA ZA'A RASA?* *WAYE ZAI TSIRA DA RAYUWARSA?* *WAZAI TSALLAKE?* *WAYE KUMA ZAI AFKA?* *Kasan irin GIRMA da adadin TUGGU da MAKIRCIN DAKE DAURE da wannan masarauta kuwa?* *Akwai wata BABBAR ALAQA dake tsakanin masarautun biyu......ETHIOPIA da AGADEZ* *Akwai wani LULLUBABBEN SIRRI......akwai wata irin BAHAGUWAR SOYAYYA ME WAHALAR GASKE cikin labarin LU'U LU'U* *WACECE MAMMINA NE?* *WACECE SAFEENA?* *WACECE MORSA SAFIYYA?* *_NEMANSA TAKE CIKIN DUHU SAIDAI BATASAN YANA DAB DA ITA BA_* *_GANI YAKE BA HURUMINSA BACE......BA DON ITA YA SHIGO MASARAUTAR AGADEZ BA......saidai bai san cewa itace RUBUTACCIYAR QADDARAR DATA SANYASHI SHIGOWA QASAR BA_* *_BATA DAUKESHI A BAKIN KOMAI BA CIKIN RASHIN SANI TAKE MASA KALLON QASQANTACCE......SAIDAI BATASAN TARIN NAGARTAR DAKE LULLUBE DA WANNAN LU'U LU'UN BA.......WANI SIRR DAKE ZAMEWA ALFARMAR RAYUWARTA A GABA_* *_TA YAYA SIRRIKA MASU TSANANIN NAUYI ZASU FARA FASHEWA?_* *_TA YAYA ZUKATAN ZASU KAMU DA SOYAYYAR DA ZATA KAISU GA SADAUKARWA?_* *_WACCE ALAQA CE TSAKANIN WADANNAN MASARAUTUN BIYU DA DUKKA BASUSAN DA ITA BA?_* *_idan har kace a nan zaka dakata.....to tabbas zan maka jaje.......wannan itace shimfidaddiya kuma miqaqqiyar hanyar da zata kaimu ga wani SHINGE DAKE DAUKE DA WATA IRIN RIKITACCIYAR SOYAYYA DA WARWARAR MAQULLAN ASIRAI DAKE BINNE A QARQASHIN QASA_* *KU KASANCE DANI A KASHI NA BIYU NA LABARIN* *ina fata baku manta da ALMAZ ba???* *NA GODE* 08187255862