💦MALIKA MALIK💦..!* _(Sai na rama..)_ *1* Free Fage   _KATSINA_      """Da misalin karfe 11:20pm na daren Ranar jumma"a Akan Titin dake tsakanin Dutsenmah da katsina wacce take gabda shiga katsina. Adaidai kan Titin akwai yan Sanda wadanda suke patrole awajen,Suna tsatsaye ne Gefe kuma ga motocinsu guda biyu akallah yan sanda zasu kai su Biyar kowannesu, sanye da uniform dinsu bakake,da ganin kayan jikinsu basai ka tambayesu ba,zaka gane dukansu inspector ne,domin basu da kowani Rank ajikin kakin nasu,dukkansu fuskarsu sanye da Hula p-cap,da bakaken safan hannu sai manya manyan Tociloli masu bala"in haske kamar ta yan fashi,wanda in aka dallareka dasu, sai ka dakata saboda bala"in haskenta,Duk motar da tazo wucewa sai sun tsaidata sunyi bincikenta saboda tsaro  dakuma bincike, wanda daga sama suka sameshi saboda masu shiga da fita da mugayen makamai wanda ake Shigo dasu daga  bodar katsinar aboye.    Motocine jere guda goma sha biyu dukkansu 11 din iri daya ne Corollahx sai babban ciki wacce tafita dabam itace Range cover baka ce gabadaya motar Tinted ne gaba da bayanta kowacce mota bayan motan an saka musu Nomba mai dauke da Tambarin *MALIKA MALIK1* har zuwa na 12,gudu suke ta shararawa bisa Titin Dutsenma zuwa katsina,Tundaga nesa Yan sandan suke Dalle su da fitila Tunda sukaga yadda suke gudun ganganci bisa Titi.      Sai da suka kawo gab kana suka fara slow,motar Farko Tana tsayawa Suma na baya suka tsaya,Wani inspector ne ya karisa kusa da motar yana kwankwansa glass din motar,sai da aka bata lokaci kana aka zuke glass din motar. Wani Inyamuri ne zaune a mazaunin Direba sanye da wasu kaya brown colour Riga da wando da alamu dai kamar Uniform ne,Kallonsa yayi daga sama har kasa kamar yadda Dan Sanda ke karemasa kallo,Cikin gadara ya furta"Lafiya mallam.?."Dan Sandan yayi mamakin jin Hausa abakinshi don akallon Farko bai yi kama da wanda yakejin Hausa ba.   Gyara tsayuwa yayi yana fadin"Zamu bincika duka motocinku ne,daga ina kuke da tsohon daren nan? kuma kuke gudu ba bisa ka"ida ba..?."Yafada yana leka motocin dake bayansa Dan ware ido Direban yayi yana fadin"kai kana ko da hankali kasan motocin waye ka tsare kuwa? dariya Dan Sandan yayi yana fadin"Wannan bashi ne Abun da na Tambayeka ba,tambayanka nake daga ina kuke,? bai mai mgana ba kawai sai ya kada kai yana fadin"Zaka shiga mtsala matukar *MADAM* Ta fahimci meke Faruwa.."Yafada kai tsaye.   Tana kishingide abayan motan Tana Karanta jaridar Dailytruth bata ma Fahimci meke Faruwa ba,sai zuwa chan Ta fahimci motar da suke ciki ta tsaya cak,cikin mamaki ta dago da kanta bayan Ta kauda jaridar lokaci daya take fadin"Joy Har mun iso gidane..?daga gaban motan ya amsa mata da fadin""A"a madam yan Sanda ne suka tsaidamu wai zasu binciki motocinmu..."Wani zabura tayi tana fadin"What...? wani banzan Dan sanda ne ya tsaidamin motoci,i swear sai na koya masa hankali sai ya gane ba"a yima *MALIKA MALIK* wargi.." Tafada cikin Fushi kafin ta balle murfin motan ta fice,Doguwa ce  sosai kirarta irin kirar Cocacola ce,Tana sanye da Riga da wando blank and white,tayi Stoking ta ciki ta Kama gashin kanta da band daga tsakiyar kanta bayan ta saki jelan Ta baya,Kafanta sanye da wani takalmi sawu ciki mai tsini sosai blak colur ne,shima Doguwar Fuska gareta wanda kusan Rabinta yake rufe dawani bakin glass,mai kyau da tsari,yadda ta fito cikin Fushi ya sanya duka bodygourd dinta suka Firfito,suna take mata baya cikin Fushi Tanufi wajen Dan Sandan da suke Rigima da Direnba Tun Farko. Ganin yadda suka nufosu ne yasa yan sandan dasuke gefe suka kariso daidai lokacin data kariso Gabansu ta tsaya suma Bodygourd din nata,sukaci burki abayanta Gilashin idonta ta cire tana fadin"Waya sakaku ku tsare ma mutane motoci,?kuma don Rashin kunya harda motocina,cikin shashancin ku,Uban waya sakaku,waye shugabanku C.P ko IGP  gayamin Shiyace ku tsare motocin *MALIKA MALIK..*? tafada cikin Tsawa Tana binsu da wani matsiyacin kallo. Jin sunan da tafada ne yasasu mamaki dama sun dade suna jin lbrinta da irin Rashin mutumcinta gashi yau sun gamu da ita,saboda kwarjinta da haibanta dukkansu sun kasa maida mata da martani balle wani cikinsu yayi magana.   Yana cikin motar yan sand'an Ta patrole video call yake Shida *YAYA MARWAN..* Hira suke sha suna dariya,ta madubin motan yake hango Abunda ke faruwa,saurin yima Marwan sallama yayi Shiko yana tsokanarshi da *INSPECTOR..* Cikin hanzari ya katse wayar lokaci daya yana bude murfin motan ya fito,dogon Namiji ne,sanye da bakaken kaya Riga da wando harda wata rigar sanyi wacce takaimai har zuwa gwiwansa,ba"a iya ganin Fuskarsa saboda ya sanya p_cap ne kuma ya sauko da ita ta Rufemai rabin Fuska,cikin takun isa ya nufi wajensu ammh duka hannuwansa suna,coge a aljihun wandonsa ne. Tana ganin ya Fito daga motan Ta nufeshi tana fadin"AU shine wannan yabaku umarnin ku Tsaremin motoci ko,toh yau zan koyamasa Hankali in yana neman na goro ne,ko na Sigari bazai kara yunkuri sawa Atsareni ba..."Tafada Tana karisawa garesa Tana zuwa batayi wata wata kawai ta kifesa da mari jikake Kau...!Saboda zafin marin saida ya fito da duka hannuwansa daga aljihu har wayarsa ta fito ta fadi bai sani ba,Hannu biyu ya sanya ya dafe Fuskarsa yana binta da kallon mamaki,miyau ta tsirtamai kafin tace"U Stupid kai ne kasa wadan nan kananun karnukan naka su tsaremin motoci ko,Dama ku yan sanda ba mutane bane,all of u,are Monkey and bakusan komai ba sai tsaida motoci kuna karban na goro dana Sigari Tunda daman ba Abunda kuka iya sai shaye shaye da yima mata Fyade ko,?Toh as From Today bazaku kara tare wata mota ba, joy bring d box Now..." Tafada ciikin Tsawa Da hanzari wanda aka kira ya nufi mota ya dauko wata yar karamar akwati yazo gabanta wani abu kawai ya danna sai Ga kudi suka bayyana dollars ne Shimfide batai wata wata ba ta dumbuza ta watsamai Afuska tana fadin"Take d money ayi na goro dana Sigari banzaye Yan"iskan kan hanya kawai,wlh i hate aikin yan sanda hardama Uniform dinsu all of dem basu da wani amfani a akasarmu sai lalacewa,Next time ka sake sakawa Atsare motocin *MALIKA MALIK..*Kagani wlh sai na saka an batar dakai Rubbish..."Tafada tana juyawa kamar walkiya Sukuma suka take mata baya.    Tunda ta kifamai mari da wadandan mugayen maganganun datake fada suka daskaran dashi gabadaya Tunaninsa da zuciyarsa ta tsaya lokaci guda,wani bakin ciki da takaichi tare da wani Fushi suka lullubeshi,kowacce kalma in ta fada sai yaji kamar saukan aradu,tacima kakin yansanda mutumci tayi jam"i gabadaya ta hada kenan harda mahaifinsa mafi soyuwa garesa,wanda yabada komai nasa domin Taimakon kasarsa,yan sanda da basa barci domin kare dukiyan al"ummah da lafiyansu sune take kira basu iya komai ba sai shaye shaye dayima mata fyade,kakin dayake burin yaga ya sanya ajikinsa Shitake kira Rubbishi...Ina!Da sake Tuni wani Bakin ciki  mai hade da wani Tarnakin hawaye suka kwaranyomishi tana gabda da Shiga mota ya daga murya cikin Fushi da amo mai Sauti yace"" *MALIKA MALIK...!SAI NA RAMA...* ..."yafada cikin wani irin amo,waigowa tayi kafin tayi danyi dariya tace"Ok start d game young police man.."Tafada kan Tafada mota,dukkansu kowa yakoma motarshi Suka tadasu suka wuce da gudun bala"i kamar zasu bankesu.   Suna Wucewa ya nufi mota yana fadin" Inspector Saleh take me to home now..."Yafada muryansa ya fara rawa  saboda bacin rai lokaci daya ya bude gaban motan ya shiga,da hanzari Inspector saleh yayi mgana da sauran yan Sandan kafin shi ya nufi motar ya shiga mazaunin direba yaja sukahau kan titin da Sauri,Suma din dai cikin katsinar suka nufa adaren. ____________________ Anguwan *LAYOUT* suka nufa daya daga cikin anguwannin masu hali dake cikin katsina ta dikko Dakin kara,kofar wani makeken gida motar patrole ta yan Sandan tayi parking Tunkafin motar tagama tsayawa ya bude murfin motan, ya Fita da Sauri yarda yake tafiya kadai zaka gane yana cikin Fushi ne da Fusata. Inspector Sale ya kalleshi yana kada kai,bai Fito daga motar ba, yamata kwana ya juya lokacin agogon dake hannunsa yake nuna karfe 1:00am na dare,shiko yana zuwa jikin get dinsu yasaka hannu ya shiga bugawa da karfi kamar zai tashi sama,megadi dake zaune gefe gyangyadi yafara dibamshi kamar amafarki yaji bugun get,da hanzari ya mike sanye da yake da uniform irin na yan mopal,koda yaji bugun bai razana ba,Nufar get din yayi yana Fadin"Who iz dis..? Tsaki yaja kafin yace *AM SALEEM FREEKING KABIR KUMO..* Yafada ransa na kuna,da hanzari jikinsa na rawa da bari yabudemai karamar kofar yana Fadin"Am sorry sir did know...."Baigama Rufe baki ba ya wucesa Fuu kamar iska baki ya rike yana binsa da kallo,domin a iya saninsa Saleem baida dabi'ar shariya. Maida kofar yayi ya Rufe yana Fatan Allah yasa koma miye ya Faru mai dadi yadda yake alfahari da wanda zai gaji Yallabai. Babbar kofar da zata sadaka da babban falon gidan Abude take,sakamakon ansan komai dare zai dawo yana Shigowa Falon babu kowa yadda yake tafiyane zai ankarar da mai kallonsa kamar agauce yake.   *CP KABIR KUMO* dake tsaye kofar dakinsa ya kuramai ido yana kallonsa yana neman Shiga dakinsa ne yasa yayi kiransa.."Saleem...."Yafada cikin datattako,Waigowa yayi da sauri yana kallon Abbin nasa,saurin sadda kai yayi saboda kada Abbin nasa ya fahimci halin dayake ciki kakalo mirmishi yayi yana Fadin"Na dawo Abbi..." Gyada kai yayi yana Fadin"Ai na ganka,ammh why naganga kamar azafafe..? Saurin Washe hakora yayi yana Fadin"la babu komai Abbi,barci nakeji dat why na dawo da Wuri.."Yafada yana Jin takaichin karyan dayayi,kallonsa kawai Abbi yayi kafin yace "Ok sai da safe.."Yafada yana kuresa da ido,da hanzari yace"Sai da safe Abbi..."Yafada yana tura kofar dakinsa ya Shige da sauri,Yana sauke ajiyar zuciya. Yana Shiga yayi tsaye yana karema dakin nasa kallo,hannu ya dungula ya daki bangon dakin,bayan kunnuwansa suna jiyomai amom muryanta,fuskarsa tana jin zafin karan Tafinta kana idanuwansa suna kallon sanda ta Tofamai miyau,ta watsamai kudi,kana kunnuwansa na jiyomai sanda tace yan sanda basu da wani amfani,sai yima mata fyade da shaye shaye? kenan harda Abbinsa tayi jam"i ? yazama dole ya binciko ko wacece wannan yarinyar domin yayi Saurin ankarar da ita kuskurenta. Kan gado yafada yana dukan katifan kota ko"ina Yana fadi da karfi..* WLH SAI NA RAMA..."!* yake Fada yana jin wani tukuki daga kasan ransa,har sai da wasu hawaye suka zubomai,yasaka hannu ya sharbe kafin yace"No saleem kuka bana ka bane,juz stand up kayi karatu tukuri domin ka zama DAN SANDA,ka nuna mata cewa ita bata karfin kowa ba,ammh duk hakan bazasu samu ba sai yafara gano ko  *WACECE ITA*..."   _*Tirkashi....Salon na dabam ne,haka Jimarin na mussaman ne,wannan karon Abun zai taba zukata,wannan karon Abun zai taba kowa ne,Kada Abun ya daure muku kai Abu daya zaku nemo Wacece MALIKA MALIK.!? kuma waye wannan Dan MATASHIN SAURAYIN? miye alakarshi da Aikin yan Sandan? Duk ku biyoni Zan warware muku Zare da Abawa*_ _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550* JAMILA UMAR GT BANK,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyi KISHIN MATA na hafnan,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488,am srry a karshen Aliyu gadanga nayi mistake wajen Rubuta nombata maimakon na saka 69 sai na saka 60😂Fata zakuman izuri jikin tsufa ne😂👌🙋 *💦MALIKA MALIK💦..!* _(Sai na rama..)_ *2* _NIGERIAN POLICE FORCE-BIRNIN RUWA ZAMFARA STATE_   """Wata babban Headquater ce mai dauke da haraba mai girma da Fadi,da ban sha"awa,ginin wajen gini mai kyau da tsari domin da Duste aka gina wajen. Daga haraban Compound din Motocin Police sunfi guda goma Fake,awajen kana ga wasu yan sanda nan na shawagi awajen daga Inspectors sai su sargent suke yawo aharaban wajen Fuskarsu kwata kwata babu Annuri. Daga cikin Babban ginin, akwai tarin Afisoci kafin kayi gaba karatsa wani dogon lungu ka isa kofar Office din Shugaban Headquater wanda Sunansa yake makale jikin wani dan Anini daga saman kofar Office din, *ACP SALEEM KABIR KUMO* naga an Rubuta da manya baki,ban tsinke da al"amarin ba,sai da kofar Office din ta wangale kanta,Cak na tsaya ina bin kayatattacen office din da kallo azahirin batu an tsara wannan office din,daga yammah wasu kujeru ne guda uku ga wani karamin center table mai kyau da tsari atsakiyar wajen,kana daga gefe ga wani karamin frigde,mai kyau da tsari,daga kudu,kuma kofar wani daki,wanda yake akulle,daga gabas,kuma wani katon Tebur ne mai dauke da Takardu da kuma Laptop,sai wasu kananun hotuna wanda suke sanye cikin Frame,sai daga chan sama kuma Hotuna ne,Farko na Shugaban kasa ne,sai daya na gwannar Jahar Zamfara,sai guda daya na Shugaban Yan sandan NIGARIA,IGP NA POLICE GABADAYA wato *IGP KABIR KUMO*.." Ashe duk wannan Abun kalle kallen danikeyi ma mallakin office din na zaune akan kujeransa irin mai juyawan ne,ta juya dashi yabama kofar Shigowa baya,juyo da kujeran yayi Idanunsa duka suna Rufe ne,kuma dukka hannuwansa suna kan kirjinsa ne,da alamun yayi Zurfi cikin Tunanin dayakeyi,baki na sake ina karemai kallo cike da mamaki da al"ajabi. Shiba fari bane Bakin mutum ne,ammh Ganin farko zakamai ka zata cewa Fatarshi batayi kama da yan Nageria ba,sai dai tafi chanchanta na yan kasar maroco,saboda yadda tahade tabada wani choculate,na kyau da tsari,doguwar Fuska gareshi sai dai tana  da dan Fadi kadan,Hancinsa dogo ne,wanda ya hade da bakinsa karami mai dauke da bakin Sajensa,wanda yakara ma Fuskarsa kyau lebensa Pick ne,yana Fitar da maiko kamar yasanya Man baki,giransa tana cike da gargarsa wanda taso ta hade da yar"uwanta haka gashin idonsa,Bude idanunsa dayayi ne yasa nayi baya ganin yadda Fararen idanunsa suka bayyana awaje,farare kal dasu gasu basu da girma na azo agani ammh suna cike da wani Sirri,mikewa yayi cikin azama yana goya duka hannuwansa abaya yafara zagaya office din yana cije baki,Ashe dogo ne sosai ammh yana da murjewa ta wadanda sukaji dadi da hutu sosai Wadanda ake kira giant,matashin Saurayi dan kimanin Shekaru 28 Aduniya,wanda akallo daya in kayimai zakayi mamakin yadda Yaro matashi mai kananan shekaru kamar sa zai iya taka wannan mtsayin,yana sanye da Uniform dinsa bakin wando da Rigarsa mai launin Ruwan Bula ammh light dinshi,daga hagu dan aninsa ne,mai dauke da Sunansa ajikin bayan gefen duka kafadunsa suna sanye da duka rank dinsa ma"ana amtsayin dayake kai ayanzu.   Komawa yayi yazauna yana Dora kafansa daya kan Daya,wayarsa ya zaro wata faskekiyan wayar Kirar Samsumg,yana latsawa kafin hotonta ya bayyana,tana sanye da Riga da wando black and white,kayan sun dameta bayan sun Fitar da duka Surarinta waje,kanta babu kallabi,illah dogon gashinta wanda ta daure atsakiya da band,ta saki jelan yayi kasa,fuskarta sanye da wani bakin glasa,yacikamata rabin Fuska,kafarta kuma wani takalmi ne,mai tsini wanda har ya Wuce misali lokaci da aka dauki Hoton tana saukowane daga matattakalan benen Jirgi,wasu Exscorts suna biye da ita su biyu kowanne sanye da Court sun saka wasu galasai Abun sai wanda ya gani,daya yana dauke da Brief case,sai daya yana dauke da wata karamar jaka na mata,kunnanta yana sagale da waya tana mgana sanda aka dauketa hoton da alamun ma bata da masaniyar sanda akayi hoton.   ""Kuramata ido yayi zuciyarsa na bugawa,Tuni hoton Abunda yafaru Shekaru biyar baya ya Shiga dawomai daki daki,har saida ya dafe kuncinsa ba dama inda ta shararamai mari,,har sai da ya Runtse ido,kamar alokacin take marin nashi,matse bakinshi yayi yana Shafawa,daidai inda ta tofamai miyau,idanunsa ya Runtse yana Sauke ajiyar zuciya yana tuni sanda ta watsamai kudi ajikinshi tana kiran aikin yan sanda da Rubish,Saurin bude ido yayi yana wani Zare ido,tsoro naji saboda ganin yadda gabadaya jijiyoyin kansa suka Fito radau,ga idanuwansa sunyi jajir kamar barkoni bayan gabadaya muscle din hannuwansa sun bayyana suna wani motsi daga cikin Abun tsoro wlh..😥 Wayar ya kifar akan teburin kafin ya mike azuciye kamar tana gabanshi yasaka hannu ya daki gaban Teburin yana huci yake fadin", *MALIKA MALIK..Sai na rama.."Nayi alqawarin sai na wulakanta rayuwarki sai na nuna miki ke ba kowan kowa bace,sai na miki matsayi tare da zati,jarumta da sadaukanta yafi komai muhimmaci,wlh tallahi sai na nuna miki mtsayin kakin yan Sanda yafi uwarki yafi ubanki da duka danginku da dukiyar dakuke takama...!!!!"Yafada yana Fitar da huci Shikadai kafin yakoma yazauna jagab yana Ajiyar zuciya. Duk tsawon wannan Shekarun daidai da Rana daya baitaba barin Abun yafita daga Ranshi ba,barci yake,cin abinci,wanka yakeyi karatu yake,driving yakeyi,komai in yana yi sai Abun ya fadomai,zuciyarsa taki barinsa sukuni daya Runtse ido ita yake gani tana tsaye gabansa tana aibatanshi tare da wulakanta martaban mahaifinsa bayan ta hada ta shararamai mari,kamar wani sa"anta yarayu cikin wadannan shekarun cike da zumar da zati na Ramuwar gayyah ga malika malik,duk iya tsawon wannan Shekarun daya kwashe baitaba yarda yabar bibiyar Rayuwar Malika ba,duk wasu bayananta da hallayanta da komai nata yana dashi kuma ko"ina zata yana da ido kanta,bai ta bari koda ta minti daya yarasa wani Abu game da ita ba,saboda ita ya chanza burinsa na zama *ENGNEARING*,saboda ita ayau yake zaune awannan mtsayin domin ya nunamata Wutsiyar Giwa tayi nesa dana Rakumi,kuma tsakanin shi da ita kamar tazaran sama da kasa ne. Da hanzari ya mike yafara tararra kayansa,Wayarsa ya maida aljihun kafin ya maida laptop dinsa ama"ajiyarsa key din motarsa kawai ya dauka ya Fice da hanzari,yana Fitowa suka dinga kamemai suna Fadin"Sir.."ko kallonsu baiyi ba iilah jefama wani daya daga cikinsu key yayi yana fadin"Close d office,..Kai kuma Sargent musa follow me,Abuja zamu yanzu.."Gabadayansu suka amsa da ok sir Safe landed.."Har yafara taku ya waigo yana kallon Sargent musa yana Fadin"Bring d key back to me sargent musa,i will drive my self juz take care, komai kenan zamu waya sai Monday,zan dawo ok.."Da kai suka amsa kafin sargent musa ya mikamasa key din motar,da sassarfa ya fice suka mara mai baya,sai da suka rakasa har wajen motarsa 320 kirar Toyota,Sargent musa ya budemai gidan gaba ya Shiga,sai da ya daura belt kafin ya bama motar Wuta rufemai kofar motar sukayi suna dagamai hannu,mirmishi yayi musu yana kara jadaddamusu su kula sosai,ribas yayi yana danna hon da hanzari megadi yazo ya wangalemai babban get din waje ya sulala zuwa waje da gudu,sanin dayayi akwai Tafiya agabanshi yasanya yasakarma mota Wuta,duk da yasan ko atsarin doka hakan ya haramta,ammh bashi da zabi dole ce tasashi yin haka domin yana bukatar isa Abuja kafin duhu ya shiga,sanda yake duba Rantsatsen agogon Fatan dake hannunsa Hudu saura kwata,jinjina kai yayi bai Fita daga garin zamfara ba,sai da ya tsaya awani masallaci yayi sallar La"asar kafin ya dauki hanyar Abuja.    ________________ _GARKI ABUJA_…   Karfe 8:30pm na dare yasaka Hancin motarsa Cikin Rantsatsiyar anguwan nasu tamasu hali,wato GARKI,wani tamkamen gida naga yana ta zuba hon,inda megadin gidan yazo da hanzari ya wangalemai get,Koda ya sulala ciki,parking space ya nufa inda ga motocin nan birjit,afake akaton haraban gidan,gidan gabadaya dauke yake da Security yan mopal,sukai su goma suna zagaye gidan,megadin da kanshi yazo ya budemai yana Fadin"Barka da zuwa yallabai.."Amsawa yayi yana Shafa kanshi Motar Ummi dake fake a haraban gidan ya kallah ajiyar zuciya ya sauke,Thank god Tunda Ummi tana gida yafada aransa,Wayar dake aljihunsa yafito dashi daidai lokacin da kiran *YA MARWAN* yafito daga wayarsa da hanzari ya daga yana Fadin" "Wai nikan Yaya marwan,bazaka iya kwana bane, batare da kaji muryata bane..? yafada yana dagama Mopal din dasuka sarama hannu,,hanyar dazai sadashi da Falon gidan,ya nufa yana dariya jin Abunda Ya marwan ke fada"Kai kai..lallenema yaron nan,daga ina kula da Amanan Abbi,sai na murdema kunni in nadawo malalacin Acp kawai"Dariya ya kece dashi daidai yana Shiga falon,tsaye yayi yana Fadin"Kai ya marwan,kullum haka kake cewa,ammh kaki dawowa u know  we all miss u ko.? yafada yana kokarin zama a daya daga cikin Royal chair din dasukayima Falon Kwanya,kawai yaji kikam ta fadomai tana Fadin "Oyoyo Ya saleem...."Take Fada Tana ihu,saboda yadda ta fadomai harsai da wayar hannunsa ta subuce tafada kan kujeran da yake kokarin zama,dagowa yayi yana riketa dakyau kunnanta ya murde yana Fadin"Yarinyar bakijin mgana ko? Baki ta bare da karfi tana Fadin"wayyo Allah kunnena Abbi,Ummi ku fito ya saleem zai karyamin kunni na, yarage min sadaki.."Take Fada tana kware baki harda buga kafa,shiko da gangan yakara murdemata kunni yana Fadin"Har yaushe ne,zan ce kidaina fadomin ajiki kai tsaye,ke bakisan kin girma bane.."? yafada yana dalle mata baki da dayan hannunsa,yana dariya yace"Dallah yima mutane shuru,ai babu mai zuwan cetonki..."Gum...!Yaji an makamai Filon kujera a keyarsa lokaci daya da Fadin"Sakarta don mai garinku kumo.."Tafada tana tsaye tana hararansa,dafe keyarsa yayi bayan ya saki *SALEEMA* wacce takoma gefe tana Fadin"Yauwa hajiya,ramamin..? tafada tana murza kunnanta saboda zafin dataji bana wasa ba. Da Kallo yabi *HAJIYA BABBA* wacce ke tsaye da Filon kujera tana Fadin"Ai Tunda naji ihunta nasan Azzalumi ya dawo,wlh duk kakoma dukanta sai naci kaniyarka acikin gidan nan,yarinya tazama budurwa ko yanzu aka kaita daki zata zauna,ammh kana jibgarta kamar kasamu jaka..? Tafada tana Hararansa again,Bata Fuska yayi yana kallon Saleema wacce hajiya ta karisawa wajenta tana fadin"Muga Fuskar da kunnan,wlh indai naga Shaidan yatsu sai yabiyamu,kowani yatsa dubu daya ne,dubu biyar dinmu ahannu,kaji da wai kuma Uwarka ce zata bimana hakki tunda lauya ce.." Tafada tana duba Fuskarta itako Saleema tana kara Narkewa tana fadin"Hajiya dubamin kunnan nan,Allah banaji sosai.."Tafada tana matso kwallah,Tsaki Saleem yaja yana Fadin"Allah yasa kidaijin gabadaya naga karshen iyayi da rashin kunya.."Hajiya ce tayo kanshi da gudu tana fadin"Ja'irin yaro kawai.."Take Fada tana binsa da gudu suka fara zagaye falon Saleema dake gefe tana dariya tayi wajen wayar Saleem nan ta iske haryanzu Ya marwan na bisa layi,dariya kawai yake ci diramar hajiya da Saleem shiya hanashi kashewa domin duk duniya babu wanda yakeso da kauna kamar family dinsa,da ihun murna Saleema tace. "Ya marwan I miss u.."Miss u too our little kiddo,ya sch..? Amswa tayi da lafiya kalau kafin tace"Ya marwan yaushe zaka dawo...? Kwalla ya Share saboda kewan Gida yace"Very Soon Little,naji Hajiya ita da megidanta suna kwamawa,ina ta dariya"Dariya tasaka tana kallon yadda Saleem yake gajiyar da hajiya da gudu itako taki daina binsa shiko da gangan yake zagaye falon yana mata gwalo,dariya saleema ta saka Tana Fadin"Wlh ya saleem zai gajiyar ma Da hajiya kashinta kaga yadda yake sakata gudu..? Da sauri Ya marwan yace"Little bari na kiraki Vid cll,juz ki haskamin nga wannan diramar kinji.."Da hanzari tace"Yanzu kuwa ya marwa mai jirgi,.."Tafada tana dariya yanke kiran yayi da hanzari ya Shiga wattsop,dayake tasan wayar Ya Saleem baya sanyamata password da hanzari ta shiga chairt dinshi tana bude data sai ga kiran ya marwan ta dauka tana Fadin"Ya marwan wacth dis comedy plz.."Take Fada tana haskomai Saleem wanda ya dage yana zagaye kujera hajiya na binshi da Filon kujera tana Fadin"Allah sa na kamaka ka gani maketancin yaro kawai.."Kan kujera Saleema ta haye tana Fadin"Yauwa hajiya ki kamasa,kin kusa,yauwa kamasa ...." Take Fada tana dariya Ya marwan saboda dariya sai da ya duka cikin dariya yake Fadin"Dan sanda yabada training na rage kitsen jikin hajiya fa.." '""Kai Saleem ungo naka nan,don mai garinku Uwartawa kake son kashemin..." Sukaji anfada daga  saman saukowa step Din benen dakin Abbi,dukkansu suka waiga suna kallon wani Dan Dattijo wanda akallah zai bama Shekaru 58 baya aduniya,ammh akallon Farko bazakace haka,saboda yadda yake dogo,kadan kadan Farin gashi yake akansa da gemunsa,Sanye yake da bakar jallabiya sai wani karamin gilashi mai karamai karfin gani,Jarida ce ahannunsa yana kokarin saukowa yake kara cewa"Saleem wlh kafita daga idona,so kake ka kashemin uwa da shanshancinka ko? Hajiya na jin haka ta zube kasa tana Share gumi ga hawaye suna zubomata tana Nurfafashi kamar mai Asthma,Saleema tayi saurin yanke wayarsu da Yaya marwan ta nufi Hajiya tana Fadin"Hajiya hajiya sannu bari na kawo miki Ruwa.."Tafada tana kunshe dariyarta,Saleem dake gefe ya tafi ga Abbi yafadamai yana Fadin"I miss u Abbi..."Turesa yayi yana Fadin"banyi kewarka ba,tunda daga dawowa zaka saka hajiya adamuwa.."Yafada yana karisa saukowa gaban hajiya ya durkusa yana Fadin"Don Allah hajiya kidaina biyema Saleem,wahalar dake kawai yakeso ya dinga yi.."Dagowa tayi tana share kwallah tace"Kabiru ka barni da yaron nan,Allah sai na mai rashin mutumci,kalli yadda yasani Gudu yanzu gabadaya jikina ciwo yake,Numfashina na Fita da Sauri Sauri,kilama na samu ciwon na Iska me ma sunanshi Saleema.."Da hanzari Saleema tace"Hajiya Asthma.."Da hanzari tace"Eh Asma,kalli kagani.."Take fada tana share zufa. Saleem dake gefe  ya kyalkyace Da dariya Haryana rike ciki yace"Bawanni Fa Asthma,Abbi kawai nasata gudu ne ta jijjiga jini,kullum tana zaune agida,kitse yazauna mata waje daya.."Yake Fada yana ta kwasa dariya ji yayi an Damkemai kunni ta baya ana Fadin"Saleem wai kunnenka na kashi ne? kwata kwata bakajin mgana,kullum kana girma ne,kana cin kasa ko.."Hannunta yariko yana Fadin"Ummi na..."Yake fada yana zagayowa ta gabanta kallonta yayi kafin kawai ya Rumgumeta yana Fadin"Nayi kewar Lauya mamata.."Yafada yana wani narkemata bayansa ta shafa tana Fadin"Nima haka my Son,ya aikin..?Tafada tana dagosa daga jikinta Yamutsa Fuska yayi yana Fadin"Ba dadi Ummi,wlh wahala tayi yawa baki ga sai Rama nake ba.."Dariya suka sakamai kafin saleema tace,"Bawani kaida wlh lalacinka yayi yawa Ya saleem..." Daure Fuska yayi yana Fadib"Waye malalacin..? Makewa tayi bayan Abbi tana Fadin"Acp Saleem kabir kumo mana.."da gudu ya bita bayan Abbi,Ummi na Fadin"Saleem kabari meye haka,zaku fara ko..? ina ko jinta bayayi zungurota yake daga bayan Abbi yana Fadin"Ki fito kigani wlh sai na Barki kwance yau zaki gane waye malalaci tsakanin ni da wanchan dan kauyen Saurayinnaki.."Abbi ne ya harde hannu akirji yana Fadin"To daketa mara kunya,ai ko mutuwa najin kunya mahaifi mallam.."Bata Fuska yayi yana Fadin"Haba Abbi yanzu don Allah sai na bar karamar yarinya nacemin malalaci in kyaleta.."Hajiya dake zaune tace"To karya tayi,ai ni inaga aikin yan Sandan ma,babanka yayi munamuna aka baka,ammh bawai don ka chanchanta ba,jarumi dayane agidan nan Marwanuna shine kadai Namijin gaske.."Tafada tana hararansa,wani Abu yazomai wuya ya juya yana kallon Hajiya rai bace"Karki kara walh..."Abbi yace"in kuma takara fa..? Yafada yana kallonsa Waigowa yayi yana wani hade rai yace"Ta kwana acell.."!,Yafada kasa kasa yadda bamai jinsa,kallonsa Ummi tayi tana dariya tace'"Mekace..? Hanyar Dakinsa yayi yana Fadin"Bance komai ba.."Dariya suka sakamai Abbi ya girgiza kai yana Fadin"Ke kuma Fito daga bayana,sau nawa zan fadamiki kifita harkan Saleem ehe...?Tura baki tayi tana Fadin"Abbi shifa ke shiga harkata.."Hajiya ta karbe tana Fadin"kaji ka dawani zence,wannan Ja"irin Da'n naka,ko ba'a shiga harkansa sai ya Shiga na mutum,ni wlh addu"a,nake Allah yabashi wata mata masifaffa,yadda zataci mana ubanshi dakyau.."Gabadaya suka kece dariya Ummi na dariya ta Wuce kichen tana Fadin"Little ni zo ki tayani kwaso abincin nan zuwa Dinner area,don rigimarku bata karewa keda Saleem da hajiya.." Jin haka yasa ta Fito daga bayan Abbi zata bi Bayan Ummi kamar walkiya taga Mutum agabanta yana fadin"Wa na kama.."Ai da gudu ta juya ta nufi sama tana tana fadin"Wayyo Ummi,kinganshi ko..? Shima agujen ya marata baya yana Fadin"Ummi ta aikeki kiman Rashin kunya,.."Taka taka sukayi sama aguje,Girgiza kai Abbi yayi yana zama kan kujera yana Fadin"Saleem,da saleema bansan yaushe zasu girma ba.." Hajiya data cicciba tatashi dakyar tace"Sai Ranar da kuka gama akidarku ta boko kuka aurar dasu,banda lalacewa yara sun balaga sun balage agida,ammh ba wanda yayi aure,shi wanchan babban kwabo,yana chan yana yawo asama,shiko wannan banda lalaci bai iya komai,sun zauna suna ta sakarci da saleema acikin gida,Allah dai ya ganar dakai kabiru.."Tafada Fuska ba Annuri kafin ta dingisa ta Shige wani korido tana ta mita ita kadai,da kallo ya bita kafin yabi Ummi da kallo,wacce ta kwaso kololi,yana kallonta ta kalleshi ta kauda kai,tana cije baki,kamar zatayi dariya,dan mirmishi yayi yana maida hankalinsa kan jaridan dayake karantawa,domin indai wannan mganar ne,Hajiya kullum sai tayimai gori,kamar shi yahanasu yin Auren,batasan komai lokaci bane. *Hohoho Fans,yanzu fa aka Fara wasan akwai kitimulmula😂tare da chakwakiya awannan KAFCHAN👌Wlh Duk wacce bata karanta Malika malik ba,taga salon Soyayyah cikin daukan Fansa ba,am srry to say ansha da ita,domin Abun zaifi daukan hankali Fiye da Amanar da HAFIZ ABDALLAH RUMA Yabama HAFSAT ATTIHIRU ATTA,Kuma zai bambamta da irin Sakacin da SAKINA KABIR KANKIA,tayi ga mijinta DR SAFWAN SALE SAFANA,Kuma soyayyar ba irin wacce NAZIR ADAM GALADANCHI ,Yanuna ma NUSIBA ABUBAKAR BUNZA,bane,Kana ba irin kaunace wacce MU"AZZAM MUHD MODU,Yanunama ZAHIRA ABUBAKAR BHAGANA,bane Kuma ba irin Shakuwa da Kauna bane irin wanda SARKI ALIYU ABDULNASEER,yanuna ma Masoyiyarsa AZEEMA LAWAL BATURE,bane✌,wannan salon zai Bambamta dako wanne,wannan zuwan Salon na ACP SALEEM KABIR KUMO NE,Dakuma MALIKA ABDULMALEEK DAN KASUWA,Kada kibari ayi baki* *JANAFTY*   *💦MALIKA MALIK💦..!* _(Sai na rama..)_ *3* *KANO* _MALLAM AMINU INTERNATIONAL AIRPORT KANO_ """Jirgin karfe 12:00pm shine ya sauke mutanen daya dauko daga birin London Acikin jerin mutane na 8 masu Fitowa *MALIKA* tana daya daga ciki bayanta kuma Amintattun Excorts dinta ne joy and peter,sanye cikin bakaken court kowanne ya toshe bakar Fuskarsa da wani makeken bakin gilas,Joy shike rike da Brief case dinta,wanda manyan bayanai game da document na kamfafonin mahaifinta ke ciki,ma"ana kowani Kundin bayanai,Shiko peter dama kullum dan Rike jaka ne da wayoyi dama aikinsa kenan. Yau din ma tana sanye ne cikin shigarta,buh na yau Suit tasaka na mata riga da sikat,Ash and white,wanda sikat din,da kadan ya wucemata gwiwa,Fararen kafafunta kal,duk suna waje bayan ta kawata kafarta da wani Ash din cover,wanda yake da dan Dudu,Yau anci sa"a bayan ta dane gashinta atsakiyar kanta ta Makaleshi da band,tasaki jelan ta baya,sai ta dora wani ash din vail,ta yaneshi daga tsakiyar kan,Fuskarta sanye da wani glass,mai duhu wanda ko kwayan idonta baka iya hangowa. Farace Tar sosai,irin Farin ne bamai launin jaja ba,Doguwa ce ammh ba sosai ba,Allah yabata wani Abu waishi tsarin hip,ga kuma madaran shanu suma babu laifi,daga tsayenta tana da Shape din,cocacola ne,Hancinta ba dogo bane sosai,ammh yadace da Doguwar Fuskarta,mai dauke da karamin bakinta,wanda yake Fari tas,shima Gashin idonta zarazara ne kamar yadda idanuwan nata keda girma,Gashin giranta ko baki silif,yana ta Sheke,. kallo daya zakamata Kazata wannan bata hada komai da Hausa Fulani ba,kai infact ma, zaka zata irin bakin nan,ne dake Shigowa Nageria harkan kasuwanci ,daga yanayin dresssing dinta da yanayin yadda take mgana zaka  Shaida tabbas wannan ko Aturawan takai makura. *MALIKA MALIK.."* Kenan Y'a kwaya daya Tak,ga *ALHAJI ABDULMALIK DAN KASUWA* Wanda saboda kudinsa da tarin kaddarorinsa da kamfafononi,tundaga gida Nageria har zuwa kashashen ketare,yasa ya zamanto cikin jerin masu kudi na hudu A kasarmu ta Nageria. Tana Saukowa daga kan Step din jirgin Tuni dama motocinta tare da Sauran Excort dinta sun zo daukanta,Duka motocin wannan karan 4matic ne,kuma 12 ne,kowane akwai tambarin *MALIKA MALIK*1 har zuwa 12 akallah excorts dinta masu tsaronta zasu kai su ashirin,kuma babu dan musulmi ko daya kuma babu jinsi mace,duka mazane kuma wasu gardawa konace samudawa,Tunkafin ta kariso suka bude mata Daya daga cikin motocin,ta Fada cikin isa da takama,nan da nan kowa yakoma motarsa suka bata Wuta sukabar Aiport din aguje,babu wanda ya damu domin indai malika malik ne kaf Nageria,yaro da babba babu wanda baisanta a Talabejin ba,in ma Mutum baita ganinta ba,to babu Shakka yasan lbrin sangarta tare da lalacewa ta malik malik,da sunan wayewa ko kuma nace GATA. ******************* _KATSINA_ *GRA*.. Cikin Gra ne Tamkamemen gidan mahaifinta yake,mai kama da yanki Guda saboda girmansa da kuma Fadinsa,inda za"ayi Estete,tsab za"a iya yin guda 40 kuma kowanne da girmansa,Hon suka zuba masu gadin dake sanye da Uniform sukazo suka budemata don sunsan hali,minti daya suka kara korace Awajenta. lokacin da motocin suka Fara sulalawa parking space,kowani Excort ya fito daga motarshi yana bin motarta da gudu bata tsaya ba,sai A babbar kofar da zata sadata da cikin babban Falonsu,Budemata sukayi jikinsu na Rawa masu,gadin kuwa fadi suke"Wlcm back madam..."cikin isa ta zuro kafarta waje kafin ta bayyana waje Fuskarta babu Fara"a  ko kadan bata kallesu ba,kawai tafara Tafiya joy da peter suka take mata baya,ajiyar zuciya sauran suka saukesu,suna Fatan yasa anrabu lafiya kenan. Tana Shiga Falon wanda ya kawatu dawasu royal chairs hadaddu masu kyau da tsari sai wani tamkamemen plasma,daya kusa cinye rabin bangon dakin,ko sallama batayi kamar ba,don ba dabi"arta bace, *HAJIYA BINTA* ,Dake zaune tana kallon Atashar Arewa24 ta dago tana kallon Malika wacce ko kallonta batayi ba,saima zuwa datayi ta gabanta zata Wuce,tasa Tudun takalminta ta murje mata kafa,Azaban da Hajiya binta taji ne yasa ta saka ihu,wanda ya Fito da Alhaji maleek da hanzari wanda ke kayatattacen Falonsa na sama yana hutawa,Dattijone don zai iya kai shekara 67 aduniya Abun mamaki baki ne silif,ammh kuma yana da kyau  da hanci,Fuskarsa tacika da Farin gemu ammh kana kallonsa zaka Fahimci Farin gemun na halitta ne ba wai na Tsufa bane,domin duk inda jin dadi da Hutu yake toh Alhaji Malek na tare dashi,don Shida iyalansa basayin wata Daya A nageria sai Sun Fita waje sun Huta. Ihun Hajiyane yafito dashi yaga ko lafiya,ammh sai ya ci karo da Malika tana kokarin karisowa gareshi da hanzari ya tafi gareta yana Fadin"Wlcm back my Sweetbbby...."Yake Fada yana Rumgumeta matseshi tayi tana Fadin"Dddylove i really miss u..."Kiss yayimata agoshi yana Fadin"Miss u more Sweetbby,yanzu mrs Suzan takirani tace komai yayi daidai.." Wani mirmishi tayimai Tana Fadin"U know me Daddy,bazan taba baka kunya."Wata Dariya yasa yana Fadin"Hhhh..Datz my Sweetbby,maza ki wuce daki kiyi wanka ki Shirya ki sauko muyi lunch.."Tabe baki tayi kafin ta cire glass din idonta tana Fadin"No not now, Daddy naci abinci a cikin jirgi,but now zan Shiga in huta sai na Fito we tok later.."Shafa kanta yayi yana Fadin"ok maza my Sweetbby ahuta lafiya karki sake kitashi sai around 6 haka kinji..?"Kai tadagamai tana bashi kiss a kumatu tace"Daz why i love u,my Daddylove much wlh.."dariya yayi kafin Shima ya maidamata da kiss din,da hanzari Ta nufi wani Daki dake kusa da Inda Abbanta ya Fito tana Shiga dakin su peter suka rufamata baya. Alhaji Malik ya kalli Hajiya binta yana Fadin"Lafiyanki kuwa naji ihunki daga sama...? dagowa tayi daga murza kafarta, datakeyi Yar matashiyar matace wacce ashekaru bazata gaza 36 aduniya ba,farace tas,ammh tana dan jiki,idonta cike da kwallah tace. "Haba Alhaji,malika ce fa tashigo babu ko sallama kamar ba yar musulma ba,kuma don rashin kunya tabiyo tagabana zata wuce hakan bai isheta ba,sai da ta takani da Katon takalminta mai Tsini.."Tafada cikin takaichi. Tsaki Yaja yana Fadin"Gaskiya Binta fitinarki da tseguminki yafara isata fa,Haba kin sakama yarinyarnan ido,ita da gidan Ubanta in bataji dadi anan ba,waje kikeso taje taji dadi ehe.."?Yafada yana tsareta da ido. Kallonsa tayi baki bude tana Fadin"Ammh tsakani ga Allah Alhaji Abunda Malika tayi yanzu ya kyautu..?"Hannu ya dagamata yana Fadin"Kinga Binta kifita daga idona indai akan Malika ne,banda Abunki nawa malika take,haryanzu fa yarinyace wani Abun sai ana nusar da ita,kuma kibar wannan mganar kada ki kuskura ki tankamata,yanzu nan sai takama Fushi,kuma kinfi kowa sanin yadda Fushin malika yake awajena Atoh."Yafada irin Abun ya isheshi haka,ya sa kai yakoma cikin kayatattacen Falonsa bayan ya saki Siririn tsaki. Hajiya Binta ta bishi da kallo tana kada kai,idonta ya ciko da hawayen takaichi da kuma haushin iyayenta da suka biyema Rudin Duniya da kuma tarin Dukiya suka kawota inda ba"a san mutumcinta ba,daga Uban har yar duk basu da mutumci babu wanda ke ragamata. Dauke hawayenta tayi tana mirmishin karfin hali,Tuna duk mutuwa ce taja mata wannan Tonon Sililin,da"ace Abban *JODA* na raye ta tabbata da bata auri Alhaji Malik ba,balle har tazama Abun wulakantawa awajensu. Mikewa tayi rike da wayarta tashige wani korido tana kwalama Atika mai aikinsu kira,domin ta umarceta ta shirya lunch bisa Dinning area. Katon Falo ne,wanda yaji kayan alfarma,Tunda tashiga tafara yadda kayanta,Tacire vail ta Wurga ta cire band din kanta,ta warware gashin kanta bayan ta Fara cire botir din Rigarta gabadaya halittun kirjinta dake jikin beriziya suka bayyana,Peter ko da joy suna tsaye kyam,don madam bata basu daman Tafiya ba,Indai Tsiraicin Madam ne,Su Tuni sun dade da haddace kamminshi don bata da kunyan idon maza,Hatta Swining pool in zata wanka tare dasu take zuwa tayi Tsirara daga ita sai pant agabansu ko gefen gyalenta. Murya ta saka tana Fadin"Merry...Dose..."Take Fada cike da Fushi sai gasu sun Bude wata kofa sun Fito da gudu agabanta suka zube suna Fadin"Srry madam...SrrrY..."Wani Wulakantattacen kallo take binsu dashi kafin ta sanya kafa ta shuri merry sai da ta kifa,lokaci daya ta gaurama Dose mari tana Fadin"U too u are Animal,.."Take Fada tana huci Baya sukayi suna kuka suna bata hakuri da hannu ta dakatar dasu kafin tace",last chance..."Bata gama Rufe baki suka mike daya tafara kokarin ciremata takalmi daya kuma tafara kokarin karisa balle mata botir din Rigarta bayan ta ciremata Coat da hannu tayi musu peter alamu, sai kawai naga sun nufi wani kofar glass,wanda sai  da ta dauki hoton Fuskokinsu ashe Na"urace awajen kafin ta bude musu su Shiga,sun Shiga ba dadewa sai gasu,sun Fito wanda kafin Su Fito sai da Na"uran tagama cajesu tsab ta tabbatar da basu tare da komai kana ta barsu suka Fito,suna Fitowa tayi directing dinsu da hannu alamar su Fita,kai tsaye suka bude kofa suka Fita,bayan su merry sungama cire mata duka kayanta,harda bra da pant tsiraranta haihuwar uwarta suka dagata tsab,sai cikin katon bedroom dinta inda katon Tiolet dinta yake,wanda yaji kayan alfarma kyace baza"a mutu ba,cikin jazucci suka sakata bayan suncikashi da wani Ruwan kumfa,Dose ce ta Fice ita kuma merry ta fara Yimata wanka tana kwance ta lumshe ido ko agefen gyalenta.. Niko nace *KUTUMAR UBAN CHAN*😿 Dose na Fitowa takoma kayattacen Falon ta kwashe duka kayanta,kafin takoma Toilet din ta watsasu cikin wani dogon kwando na tara kayan wanki,Fitowa tayi kafin ta isa wani makeken Abu wanda ke dauke da glass,ashe Na"urace Sai da Ta tantance Fuskar Dose kafin wata yar kofa ta bude,Kayane jere cikin tsari iya kallonka mallam,dogayen Riguna,riga da wando ne,suit ne mini sikat da mini wando,Duk sagale cikin hanger,kai kace ka shiga bouitque ne,Wata yaloliyar Doguwar Riga ta daukomata wacce marabanta da Tsirara kadan ne,saboda tasan yanzu barci zatayi kuma iyakarta gwiwa,ta Fito mata dashi kafin kuma wajen ya Rufe kansa,Sun dauki tsawon minti talatin atiolet din kafin Dose ta kuma suka daukota wacce suka nannade da wani katon Towel,suka zo suka ijyeta kan wani dogon Stool,ban gama mamaki ba,sai da naga tana ta Shafemata da mayuka masu tsada itako tana zaune idonta na lumshe,har tagama ta fesheta da body sray,Dose ta matso kusa tana gyaramata zaman gashinta wanda yadan jike kadan da Ruwa,tana kokarin kunna Hand drayer,ta dakatar da ita,da hanzari ta dauko yar Rigar data dauko ta ziramata wacce ta Fito mata asalin tsarin kirjinta,tunda babu bra babu pant,Dose ita kadai ta dagata bata sauketa ako"ina ba sai akan wani gado,mai kama da alkaki saboda yadda yake amulmule,wani karamin Filo fari dake gefe ta Rumgume tana lumshe ido,Katon blanket ta dauka ta Rufamata shi har zuwa Kanta Gefe suka koma ko motsi basuyi suma dana kallesu suna sanye da Riga fara,sai bakar biri da wando,sai Hula akansu kace wasu ma"aikatan hotel,sai da tasha iska kafin tadaga  musu hannu,da hanzari suka kada kai suka Fice suka jawomata kofar,nan kowaccensu ta maida hannuwanta abaya,domin akidar madam in tana barci babu mai tashinta sai ta tashi da kanta,kuma zata iya bukatan wani Abu,kuma in tamaka kira daya baka zo ba,korace sudinma tana daga musu kafa ne don tana jin dadin zama dasu.    _________________ *ABUJA* ""Duka iyalan gidan sun hallara bisa babban Dinning area,mai kama da Fili guda,ajiyane da daddare suka kara samun Zuwan wani dan gidan,bayan Saleem,wato Ya marwan wanda yake aiki alagos,Zaune suke dukkansu suna breakfasrt suna dariyan hajiya wacce ta sanya kujeranta kusa data saleem,Ummi na kokarin saving dinta,tayi Saurin Tsoma hannu a filet din gaban Saleem,wanda yake cike da Soyayyan dankali da kwai,bata Fuska yayi kamar yayi kuka,itako hajiya ta cika baki hartana maida Saura a Farantin,Ummi tana Dariya tace"Hajiya ki barmishi kayanshi bari na zuba miki naki..".. Hajiya ta gyara zama tana Tsungulin Saleem tace"Barni Aisha yau tare da Ja"irin nan zan karya.."Tafada tana kara saka hannu ta cika baki,har miyau dana baki suna biyowa,Kauda Fuska Saleem yayi yana Fadin"Na Shiga uku Ummi,kalli harda miyan bakinta take sakamin.."Dunguremai kai tayi tana Fadin"An saka din,don kaniyarka,Wlh in kaja tsiya zan maka kaki yanzu nan,kuma wlh na matseka saika hadiye,.."Tashi yayi da Sauri yana kakaro amai,tako damke hannunsa gam,taki sakinsa,Ya marwan dashi da Saleema suna ta tsintsiran dariya Abbi na zaune yana kallonsu,don yasan koyayima Hajiya mgana baji zatayi ba,Ummi ko bata saka baki ba,sanin halin hajiya in Tafara Abu bata iya bari,Saleem din ne kadai mganinta. Gani yayi tasaka karfinta tana Rikeshi tana neman ta maidashi inda yatashi,Ganin haka yasa ya rike mata hannu yana Fadin"Sakarni kiji wata mgana.."Hararansa tayi tana gyara daurin dankwalinta tace"Anki din,ni zakama wayau,ai wlh yau in har ba lbrin kasamu matar aure zakamin ba,ko ubanka kabiru bai isa ya kwaceka ba,sai kasha majina na.."Tafada tana kebe Fuska,Ummi ce ta rike baki tana bin Fuska Saleem da kallo... Shuru yayi yana bin Hajiya da kallo kafin yace"Really,,? kina son nayi aure kenan hajiyata..,?"Jin haka yasa ta washe baki cike da goro tace"Sosaima Haba Salihu,kunfa girma kungama balagewa asannin haihuwarku a kumo harda masu mata biyu,bama daya ba.."Rausayar dakai yayi yana Fadi cikin Ransa" Dis iz d right Time...."Yafada kafin yakalli hajiya yana Fadin'",kamar ko kinsani Hajiya mganar auren ce tadawo dani wannan weeked din.." Kowa dake wajen yadauka yanamata wasa ne don ta sakeshi,shiyasa harda Ummi amasu dariyan,kura masa ido tayi kafin tace"Da gaske kake Salihu..? Gyada mata kai yayi kafin yace"Eh da gaske nake Hajiya ina son kisa baki Abban yaje nema min auren yarinyar danike so.." Jin yadda yayi mganar babu alamun wasa yasa kowa yadaina dariyan dayakeyi hatta Abbi dake ta cin abinsa sai da yadago yana kallon Saleem,wanda ya kurama waje daya ido,Jansa kan kujeran daya tashi Hajiya tayi bakinta yaki Rufuwa tana Fadin"Alhamdulillah Allah yakarbi Addu"a ta,to maza ga kabirun nan,sanar dashi wata yarinyace,Allah sa dai yar gidan Mutumci ne..?Bai wani Damu ba kai tsaye yace""Ba wata bace illah Diyar shahararran Dan kasuwan nan wato *ALHAJI ABDULMALEEK DANKASUWA*..." Gabadayansu suka razana da jin zencensa saleema data tura chips abaki sai da ta Furzoshi waje,Shiko Ya marwan,yakafa kai yana kurban coffoe,sai da ya kware yafara Tari sama sama,Ummi dake zaune sai da ta mike hannunta dafe da kirji shiko Abbi kasake yayi yana Bin Saleem da kallo,wanda yayi saurin boye razanar daya ga sunyi Afuskarsa. Saleema ce cikin Rudani tace"Ya saleem Wai wakake Nufi..? Kai tsaye yace mata.." *MALIKA MALIK.."*...Da ita da Ya marwan sai gasu tsaye suna zaro ido atare suka Furta..",Bura uban chan..." Suka Fada suna kallon Saleem kamar wani tababbe,Hajiya datake nazartansu tace"Kai wai miye haka daga Fadar suna,kun shiga Rudi lafiya meyake Faruwa ne..? Ya marwan ne yace"Komai ma yafaru Hajiya bakiji sunan daya Fada bane..?Tabe baki Hajiya tayi tana Fadin"Wannan bai dameni ba,indai yar gidan mutumci ne,Amemasa aurenta Tunda yana Sonta.." Wani kallo Ya marwan,ya ke Wurgama Saleem,wanda yaki bada damar Ya kalleshi balle ya Fahimci wani Abu,To waima yaushe Saleem yataba haduwa da Malika,yarinya da Da Namiji ma baya gabanta? Bai gama mamaki ba yaji saleem na Fadin"Nidai hajiya gashi na kawo wacce nake so don Allah ki matsawa Abbi yaje gun mahaifinta ya neman min Aurenta,kuma one anoder thing,don Allah Abbi karka sanar dasu Aikina,ka sanar dasu ina aiki da hukumar costome ne,in komai ya daidaita zan sanar da ita dakaina plz Abbi.."Yafada yana hada hannuwansa kafin ya Ture hannu Hajiya dake Rike dashi ya Nufi hanyar dakinsa da sassarfa Saleema da ya marwan suka bishi da kallo baki sake. Hajiya ce ta kalli Abbi,wanda yacigaba da karya wasan tana Fadin"Kabiru maza ka hanzarta,Tunda daga jima kasan mahaifinta Tunda kaima babba ne agwannatin,Tunda har ya nuna yanaso to gwara agaggauta yimai kaji ni ko bakaji ni ba..?"Batare dawani Tunani ba Abbi yace"Insha Allahu hajiya zan kira mahaifinta awaya mufara mgana dashi abokina ne,tare mukayi Dan Fodiyo dashi ammh bayan mungama Zumunci yayi Rauni.." washe baki Hajiya tayi tana Fadin"Kajima ko,to maza kabar zencen kira zuwa zakayi don wannan mganar bata waya bace.."Gyada kai yayi yana Fadin"karki damu hajiya komai zai daidaita.."Hajiya na murna tana ta sakama Abbi albarka,Ta mike tana kallon Ya marwan tace"Andai ji kunya babban banza,har kaninka yafika sanin ciwon kansa,kadai je,kayita yawo a iska haka zaka zo ka koma,wlh in ka mutu,ana sadakan uku zan saka asallami kowa,daganan kowa ya manta dakai,Tunda ba wani mgaji gareka ba,balle akalleka Atuna ka"Tafada tana Wucewa rai bace. Ummi dake zaune takalli Abbi tace"Yallabai kako gane wata yarinya Saleem yake mgana..? Hannu yadagamata yana Fadin"mubar wannan mganar Aisha zamu tattaunata letter.."yafada hankalinsa kwance. Ajiyar zuciya Ummi ta sauke kafin ta mike tahaye sama ranta bace,Saleema tabi bayanta aranta tana Fadin"Lallema ya saleem,ya daukoma kansa dala ba gammo,inma ta yarda zata aureshi don ita ko Qur"ani aka bata zata dafa ta karyata Cewa Ya saleem da malika malik suna soyayyah macen da bata san Darajan kanta bama balle hartasan da wani.."Saleema tace afili"kilama ta girmeshi wlh, yarinya kamar arniya wacce bataga Ruwan musulunci ba"Tafada tana bin bayan Ummi da Sauri taje tasanar da ita kamar ta wahalar da kanta bazai samu damar Auren wannan yarinyar ba,. Shiko ya marwan bayan Saleem yabi koda yazo dakinsa sai ya tarar da ya rufe da key,jinjina kai yayi yana fadi Cikin Ransa"Ka Rufe kan ka mana,Tunda karasa wacce zaka Furta zaka aura ko wasa ne,sai wannan watsatsiyar yarinyar.."Yafada yanajan tsaki ya wuce dakinsa,yana ayyana tabbas akwai yarinya haryanzu Atare da saleem.... _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 *Janafty..* *💦MALIKA MALIK💦..!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 Free Page *4* *FLASH BACK*      ""*IGP KABIR KUMO* Shine asalin sunan mahaifin Saleem,wanda ya kasance haifaffan garin gombe ne, a KUMO babbar hukumar *AKKO LOCAL GOVERMENT* Kabir ya fito daga gidan mutumci da tsatso mai kyau da Asali,family dinsu basu dawani yawa sosai,ammh suna da kudi dayake suna da manyan yan boko sosai kama daga Doctoci zuwa sama.    Sunan mahaifinsa BASHIR,Wanda ya kasance Lacra ne,a babban jami"ar gombe kafin Allah yamai Rasuwa ya rasu yabar matarsa *HAJIYA HAFSAT* da Da'nsa kabir,wanda yake aji uku ababbar jami"ar Usmam DanFodiyo Universtiy Sokoto inda yake karantan Sciology Sanin Hallayyar dan Adam kenan. Mutuwar mahaifinsa ta girgiza sa ammh haka ya fauwalama Allah komai ya maida hankalinsa akaratunsa,Shigansa jami"ar ne suka hadu da *ABDULMALIK SA"AD wanda shi yake karanta Business Admistration,ammh dayake hostel dinsu daya yasanya sukayi abota sosai Duk da shi Abdulmalik din dan jahar katsina ne akaramar hukumar MALUMFASHI.   Kammallah karatunsu shiyayi sanadiyar raba zumuncinsu domin Shi kabir daganan Burinsa dama Aduniya ya ganshi yana sanye da kakin YA'N SANDA,nan da nan yasamu nasarar Tafiya *POLICE STAFF COLLAGE JOS PLEATUE* makarantace dake horar da manyan ya"n sanda mussaman wadanda aka dauka daga matakin Degree,shekara daya yayi ya Fito amtsayin *ASP*   lokacin ne,kuma yayi Aure da yar"uwansa AISHA,Wacce ta kasance diyar wan babanshi ne uwa daya uba daya aka hadasu zumunci lokacin itakuma tayi candy,sai ya taho da ita nan ZARIA inda akayi posting dinshi,har yayimata cuku cuku ya sanyata a ABU Kongo,tana karantar Sharia Low,Shekaranta biyu tagama lokacin kabir yasamu chanji wajen aiki,zuwa kano suka tararra suka koma inda tadora daga Karatunta a low sch kano,Shekararta ta Farko Allah ya azurtata da ciki,inda ta Haifi danta na Fari  Wato *MARWAN* Shekaran Marwan biyar Aduniya ta sake haihuwan Danta na Biyu Wato *SALEEM* Lokacin kuma Kabir yana matsayin *DEPUTY COMMISSIONER OF POLICE* Na jahar katsina. Sai da Saleem ya shekara Hudu Aduniya kana aka haifi *SALEEMA* wanda daga ita Allah bai kara bata haihuwa ba,kuma bawai don ta tsayar ba,Allah ne ya tsaidamata,Tunda daga ita har kabiru,suna bukatar ya"ya sosai atare dasu lokacin ta kamallah karatunta na low school ta Fito da sakamako mai kyau sai Kabir ya nema mata aiki ababban kotun jaha dake katsina nan da nan tafara aikinta amtsayin Lauyan gwannati. Tun Marwan na dan karami yake da sha"awan Zama matukin jirgin sama wato pilot,shiyasa yana gama secondry sch dinsa Iyayansa suka Turasa Kasar Russia,domin karantan Abunda yashafi Tukin jirgin sama,wanda zai dauki kimanin shekaru biyar achan,lokacin Saleem da Saleema,duk suna Nagerian Turkish Acadamy Abuja,Saleem na jss2 ne,Saleema na primary 4,ko lokacin tafiya Marwan Hajiya hafsat mahaifiyar Kabir taso ta nuna gaddama ammh iyayan suka lallasheta suka nuna,kamar yadda suka gini da boko to suna Fatan suma iyalansu sun san ilimin Addini hade dana boko,wanda malami na mussaman garesu,mai koyar dasu karatun Addini,Saleem dai ya sauke alqur"ani Tuni,Sauran littafai yake bita yayinda Marwan yasa wasa har kaninshi yazo yawucesa. Tun bayan haihuwan Saleem da tasowarshi mutum ne mai kulafuncin iyayansa,mussaman ma Abbansa,wanda suke kira Abbi,duk inda zashi yana makale dashi shiyasa dayawan abokan mahaifinsu sunfi sanin Saleem akan Marwan saboda shi nanike yake da mahaifinsa,shiyasa ko affice zashi dashi yake zuwa tun yana karami saleem yake jinjinama masu sanya kaki kowani iri,lura da ganin yadda mahafinsa ke kokari da fadi tashin kare hakkin al"ummah,Tun Abun na bashi sha"awa haryazo yana burgesa,ammh baitaba jin zai iya zama kamar mahaifinsa ba,shi arayinsa yafison zama *ENGINEARING* Lokacin dayayi Candy lokacin ne mahafinsa yazama Commissioner of police na jahar katsina,shikuma ashekaran ne yasamu addmission a ABU ZARIA inda yake karanta Chemical engenearing,Ammh duk sanda suka samu hutu yana dawowa gida ko kuma ya Wuce kauye kumo wajen Kakarsa wacce suke kira da Hajiya babba,ko yaje da niyyar yin sati,to dakyar zaiyi kwana biyu,ya wuce katsina saboda yadda basa shan inuwa daya da Hajiya babban,saboda sa idonta,shikuma tsokana da neman Fada itakuma ba hakuri sai suyita bugawa har sai ta gaji ta kira mahaifinsa awaya tana kuka tana Fadin ya kira dansa yasanar dashi ya barmata gida ko wlh ta fita ta kira samari majiya karfi awatsamatashi zuwa waje,Cp kabir sai ya hau bata hakuri nan da nan sai yakira saleem ya Rufeshi da fadan Maza yatattara kayansa yakoma mkranta,haka zai tatattara ya wuce katsina in ko taga yadade baizo ba ta dinga mita kenan tana cigiyarsa wai duk yafi iyayansa son zumumci. In yakoma katsina hutu duk inda mahafinsa zai sanya kafa,shima zai sanya,Hardai Abbansa ya bude baki ya tambayeshi koyana Sha"awar zama kamar shi ne"Girgiza kai yayi kafin yace"Ko daya Abbi,kawai kuna burgeni ne kona ce kuna bani sha"awa bama kuba,duk wasu masu kaki dake kokarin kare hakkin mutane da kuma martaba kasarsu,suna burgeni Abbi.."Tundayaji haka daga bakin dansa ya tabbatar da cewa Allah yabashi da mai hikima da kwazo,kuma yasa aranshi ko bajima ko ba dade,sai Saleem yazo yana sanar dashi ya sanyashi aikin dan sanda,saboda yadda yasan komai na mahaifinsa ya sanya ya saba da yawa daga cikin sargent da Inspectors din,wata rana ma in zasu pertrole yakan bisu,suje tare koda bazai yi komai ba,ya zauna amota yana charting Ko Vidion call shida ya marwan,wanda yake tsokananshi sa *INSPECTOR* Yana Final year dinshi Ajami"a Incident dinshi da *MALIKA MALIK..* yafaru,Wanda Ranar ana partrole ne atsakanin Titin shiga katsina zuwa Dutsenma,wanda ake binciken mota zuwa mota saboda masu Fitar da makamai ta bodar katsina,shine fa Saleem ya bisu lokacin yana da Shekara 24 Ne Aduniya,yazama saurayi sosai,duk da kana kallonsa zaka Fahimci alokacin yanada kurciya,Tunda ga lokacin da Abun yafaru Saleem yaji bakincikin da baita shiga ba,ya shigeshi dalilin mganganun Malika,wanda sune suka sauyasa daga yunkurin zama injiniya zuwa yunkurin zama *DA'N SANDA* Ko barci yake Abun na Fadomai arai,saboda yadda yasanya Abun ranshi,ko abinci kirki bayaci koda yakoma mkranta ga karatu ga Damuwa,duk sai kafin su kare Final exams,dinsu sai yayi rama daya koma gida haka iyayansa suka tasashi da tambayan meke Faruwa dashi ammh yaki sanar dasu komai,Lokacin daya je yasamu Abbi da mganar Shiganshi aikin yan Sanda,yayi Farinciki ya Rumgumesa yana murna da hakan bai tafi Police staff collage ba sai da yadawo service kan lokacin kuma ya sanya wani Dan sanda mai suna inspector sale,wanda yakasance ya yarda dashi sosai shiya sanya amtsayin wanda zai binciko masa lbrin malika malik,Tunda farko har karshe bayan nan,kuma yasakashi amtsayin wanda zai dinga bibiyan duk wani motsinta. Tafiyarsa police staff collage Jos,cike yake da jarumta da kuma buri,in akace buri toh ana nufin RAMUWA domin yayi alqawari sai yasaka malika kuka da idanuwanta,sai ya azabtar da ita,sai tayi kukan zuciya Fiye da wanda yayi sai ya nunamata cewa ba kudi bane kadai martaba Aduniya ba,Dan adam ma kanshi Abun darajawa ne,Saleem bai da aboki ko Amini,saboda shikanshi bai yarda dakowa bane,Duk duniya bayan iyayansa sai yan"uwansa bai iya zama yayi dariya dakowa ba. yana da taka tsantsan da Duniya,miskili ne sosai mara mgana da Fara"a,ammh kuma yana da barkwaci in yaso,musasaman shida sakonsa saleema,wanda in yadawo hutu,itama tazo andinga kwamawa kenan,har hutun ya kare kowa yakoma inda ya Fito Ummi kuwa har saita gaji da raba Fada kamar mayaka,ammh bai hana anjuma ka gansu tare,Ya marwan Ya dawo Nagaria,shekara biyu kenan,yana Lagos yana aiki saboda yanayin aikinsu ashekara baifi yazo gida sau uku ba. Shekara Biyu Saleem yayi yafito amtsayin ASP Lokacin kuma aka zana sunan mahaifinsa amtsayin *ASSISTANT INSPECTOR GENERAL OF POLICE* Shikuma Saleem akayi posting dinshi zuwa kankara dake garin katsina saboda yadda yake da kwazo baima shekara ba yasamu karin girma zuwa *DSP bai Rufe wata Shidda ba yasamu karin girma zuwa *SP* Wanda lokacin ne mahaifinsa shima yasamu karin girma zuwa * DUPUTY INSPECTOR GENERAL OF POLICE*,Suka tattara suka koma Abuja,duka iyalanshi harda Hajiya babba wanda dakyar ta yarda takoma don tace tafi sabawa da kumo.   Yana da Shekara 28 Aduniya yasamu karin girma zuwa *ACP* akayi posting dinsa zuwa babban headquater yan sanda ta jahar ZAMFARA,wanda ko wata baiyi da samun karin girman ba,Allah yayima IGP rasuwa alokacin, nan da nan aka zama sunan mahaifinsa wato KABIR KUMO amtsayin INSPECTOR GENERAL OF POLICE* na kasa baki daya,inda suka tararra suka koma cikin katon gidansu mai kama da aljannar Duniya dake garki Abuja. lokacin ne kuma dukkan zati da haiba ta cikakken Namiji ta bayyana ga Saleem,wanda ya girma da buri da kuma Ramuwa ga Malika,shekaru biyar din nan duk yayi su ne cikin Shirye Shiryen Ramuwa ga Malika,kuma daman yanzu Ne lokacin daya dace ya aiwatar da kudirinsa,yasanar da kudirinsa gaban kowa da kowa ne,mussaman Hajiya babba,saboda Abbi yadauki Abun da muhimmanci,duk da shi Abbi yataba sanar dashi mahaifin malika tsohon abokinshi ne,zununci ne yayi Rauni tare kuma haduwa datayi Wuya. Ayanzu haka Saleema na aji uku a jami"ar Bayero University kano,tana karantar medicine tazama budurwa itama sosai,kuma Tana da Saurayinta *ABUBAKAR SADEEQ*Wanda ake cemai Sadiq dana ne ga wanda suke ya"ya maza da IG Kabir kumo,ammh mahaifinshi yadade da rasuwa kusan ma rikonsa Duk hajiya babba ce tayishi kuma duka wahalan karatunsa Abbi ne yayishi harzuwa yau dayake Matakin Controller,domin ma"aikacin costumer ne,yana Abia yana aiki shima bai cika zuwa gida sosai ba. Dashi ne kadai nasan Saleem nada kayakyawan alaka,sosai domim ko Hutu yazo daki daya suke kwana,ammh koda wasa Saleem baitaba sanar dashi Abunda ke ransa ba ko damuwarsa,duk sun shaku da juna sosai,sai dama Sadeeq din ya Furta soyayyarsa ga saleema ne ma yasa yadaina shigemai saboda gudun raini,dayake kuma shi Abun shi zuwa ne,Ranar dayake jin barkwamci kaf,gidan nan sai sunji ya gunduresu musssaman ma sufara tsiyarsu Shida hajiya wanda baya mutuwa kamar cin kwan makauniya. Tuni Sadeeq ya Fahimci Saleem nada damuwa,yayi tambayan Duniyan nan,ammh Saleem yacemai babu komai,domin yayi alqawarin babu wanda zaisan Abunda ke ransa sai ya aiwatar da Abunda ya kudirta Shekara da Shekaru,Saleem yana da zuciya sosai da kuma tsantsane ya tsani mutum wanda baisan darajan manya ba balle kuma wanda baisan darajan mutane ba,Yana da tsanani a kan ra"ayinsa in yakafe kan Abu mawuyaci ne kikaga ya dawo ga Abun nan,Kallon daya zakamai ka Fahimci ko yana cikin kunci ne,saboda baya gayyatoma kanshi Fuskar dariya ko Rahama akallon farko,sai ka zauna dashi ,yana da Kawaici da hakuri,ammh baya kaunar mutum mai cin zarafi mutum dan"uwansa,Lokaci daya Malika tasamu girbin tsana mafi girma aransa,wanda ko barci yake yana mafarkinta sai kaga ya farka yana Fadin *MALIKA MALIK..*Sai na rama.."Sai daga baya sai ya Fahimci tsabar yadda yasa ka Abun ranshi ne,kuma ya fahimci Abun bazai taba gushewa ba,sai ya nunama malika iyakarta,bai gama jin ya tsani rayuwar kudi da wayewa ba,sai da yaji duka Tarihin rayuwar malika yaji yakara tsanarta da kuma kyamatanta,da duk wasu hallayanta,kana yayi tir da Mahaifinta domin bai bi Turba mai kyau b wajen samar da ita kanta Malikn ba,,kwata kwata ba macen aure bane,ba macen mutumci bane,Aranar dayasamu lbrinta yakwana yana Tunanin mafita Ada yaso ya Ci ubanta batare da alakar aure ta Shiga tsakaninsu ba sai ya duba da ita malika bazata damu ba,domin dama bata daraja kanta ba, balle tadamu don wani ya banzarta da darajanta,babban Abun damuwar mutumcinsa da kuma mutumcin Family dinsa,tare da tarbiyan da Abbi da Ummi suka basa,mezai ce musu in har ya aikata wani barna,wanda bai kamata ba tabbas wajen Ramuwa,shi zai kashe kansa bayan yabarma zuru"rsu abun fada na har abada,shikuma yayi watsi da mutumcinsa,don duk Duniya babu Abunda Saleem yafi darajawa kamar LOKACI DA kataba MUTUMCINSA. shine dalilin da Yasa yayanke shawarar aurenta duk da shikanshi in ya tuna hakan sai ya tsani kansa,ammh bashi da mafita ne sai ta hanyar aure,yadda zai ci ubanta dakyau bayan ya nunamata cewa duk wanda yataba kakinsa ko yaci zarafin wani ko yataba mutumcinsa wlh tallahi bazai taba kyalesa ba. Baya da ra"ayi zama agidajen gwannati wanda take ba ma"aikatan ta, gidanshi ya siya wani Dan daidai mai dauke da Flat biyu sai haraban farfajiya wajen adana motoci,nan bayan Headquater su ne,a anguwn Birnin ruwa. Wannan Shine.    ________________________ *WACCE MALIKA MALIK..*   """*ALHAJI ABDULMALIK DAN KASUWA* Shine asalin sunan mahaifinta wanda ya kasance bakatsine wanda ya Fito daga jahar katsina A karamar hukumar * MALUMFASHI*. Alhaji Abdulmalik,yataso ahannun kakarsa ne ta bangaren uwa,sakamakon maraya ne,duka iyayansa sun rasu Tun yana karami,ya taso ahannun kakarsa mai suna INNARO,wacce ita silam sangarta da kuma rashin kwaba da Alhaji Abdulmalik yataso dashi tun yana yaro,sakamakon gidansu irin gidan gandun nan,kowa Abunda yaga dama Shiyakeyi,gabadaya gidan yayi suna arashin tarbiya da Sanin mutumcin manya kawunanshi ma haka sukeyi shiyasa shima yataso awannan Turban,inda Allah ya taimakeshi innaro batayi wasa da karatunsa ba,dayake kafin mutuwar mahaifinsa dan kasuwa ne sosai yana da Abun hannunsa,to tun da aka raba gadonshi innaro take juyamai dayake itama irin yar Duniyan nan ne babu Ruwanta duk wata kasuwa dake ci ranaku duk tasansu,to dashi take mai hidima har ya kammallah sakandiri sch dinshi ya wuce jami"ar Usman DanFodiyo University inda yake karantar Business Admistration,domin tun yana karaminsa yana da burin zama gawurtattacen dan kasuwa,wanda zai tara kamfonino ya dinga harka Da turawa duniya tasanshi. Zuwanshi mkranat ne,suka hadu da IGP KABIR KUMO,Har sukayi abota na tsawon lokacin da suka dauka suna mkarantar dayake kuma dukkansu kowa kwaro ne adepartment dinshi,shiyasa sukayi zarra,amakarantan kowa yasansu,ko alokacin Kabir yana yawan yimai Fada in yaga sun Fita ammh lokacin sallah yayi kowa yatashi yana barin jikin zuwa masallaci,ammh banda shi,toh ganin kabir nayimai Fada ne yasa yafara kokarin gyarawa ammh na ganin ido ne,indai basa tare,Abdulmalik bai damu da yin sallah akan lokaci ba,wani lokacin sai yazo barci zai hada su duka gabadaya,ga shi bashi da ilimin addini,ko kadan ko sallar ma nashi akwai gyara,shidai kawai Babu Abunda yasani sai yayi karatu yazama yawani mai kudi ,duniya tasanshi yayi gina gida mai kyau da tsari,ya kuma auri mace kyakyawa kullum burin Abdulmalik kenan gama karatunsu shi yaraba zumuncin dake tsakaninsu,domin tun suna gabda gamawa Kabir ya lura sam Abdulmalik yarage sakamarmai Fuska kuma yarage shigemai kamar da,saboda yana mai Fada da nasihan yabi Duniya ahankali,shiyasa da suka gama mkranta bayan Kabir yatafi police staff jos sau biyu sukayi waya da Abdulmalik inda yake sanar dashi yasamu schoolarship daga gwannatinsu,zai tafi kasar England achan zai yi master dinshi,fatan alheri Kabir yayimai,toh Tundaga lokaci babu wanda ya sake neman kowa domin Abdulmalik na zuwa kasar England ya chanza layi kuma baida contact din kabir din Shiyasanya basu kara jin juna ba. Zuwanshi kasar England itace mafarin komai ba,domin Tunda Abdulmalik ya Shiga cikin Turawa shikenan Burinshi yakaru,yayi budewar ido sosai mussaman da mata,sai dai Abu dayane Allah ya tsareshi baya neman mata,sai dai iyakarsa ya tsaya iya Romance da Abun da ba"a rasa ba,ammh bai yarda ya zama mazinaci ba,yayi kokarin maida hankalinsa kan Abunda ya kaishi har ya kammallah master dinshi,akuma shekaran ya dora da phd dinsa duk akan harkan kasuwanci,akuma alokacin ne yafara aiki da wani kamfanin Turawa na sarrafa takalma,ko shekara baiyi ba akamfanin suka samu lambo yabo,saboda yadda ya jawo musu kasuwa da suna sosai aduniya Tuni Abdulmalik yaji kanshi yayi sama balle da kamfanin ta shiryamai taron godiya tare da wasu kyautan kudade,da kuma dorashi amtayin Md na kamfanin alokacin. Juliyat tana daya daga cikin ma"aikatan wannan kamfanin,wanda Tunda tasaka idonta akan Abdulmalik taji duk Duniya babu wanda takeso sama dashi,ganin yaki bata fuska sai tayi ta amfani da kissa da kissina irin na mata har yafara kulata da sunan aiki,sunyi tsawon wata Shida suna Abota kafin ta rikide takoma soyayyah mai zafi,basu Rufe Shekara ba sukayi aure,wanda dalilin haka sai da yayi alqawari da iyayan Juliyat cewa bazata taba chanza addini ba,kuma ya yarda saboda shikanshi ilimin Addinin bai gameshi ba balle yagane illah dayayima rayuwarsa. Sunyi aure tatare a gidanshi wanda kamfani ta mallakamai,watan su goma da Aure Juliyat ta haifi yarta mace,wacce tasha wahala sosai wajen haihuwarta,wanda sai da akayi mata C.S cikin ikon Allah juliyat batayi tsawon rai ba don ko Abunda ta haifa bata gani ba,Allah yayimata rasuwa,mutuwa data girgiza Abdulmalik sosai,kwanaki akayi ana shagali kafin abunne gawan Juliyat,itakuma Jaririyar data haifa sai ya mikata ga mahaifiyar Juliyat wato MADAM DORA,ta riketa kafin yadawo daga Seminar da zashi wanda kamfaninsu taturashi har kasashe uku,zai dawo nan da wani lokaci,ta karba tana kuka domin yarinyar babu inda tabaro uwarta Juliyat,ranar da zai tafi ya sakamata Suna *MALIKA* _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... _plz and plz zan Roki wata alfarma masu yiman VTU,Ko Tranafer don Allah su bari gamai bukatar Siyan Littafin malika malik,kai tsaye ya Turomin ta account Nombata 0552179550 JAMILA UMAR Gtb,ko kuma kai tsaye Amin mgana ta Wannan Nombar 09069067488,Aturo creadit kai tsaye bayan andauki Hoton katin,ina maraba daku masoyana na gaskiya_ *JANAFTY* *💦MALIKA MALIK💦..!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Dedicated to my Sweet Dota *RAHMA ABDULNASEER NIGER* 😘Ladingota ikon Allah...,Allah ya albarkaci rayuwarki D'iya Ta gari🙏,endless of love Dota_😘💖💕 *5*    ""Bai waiwayi Malika ba sai da tayi Shekara hudu aduniya,ammh duk bayan watan Duniya yana Turamata over 5k abankin madam dora domin hidimarta,shiko bashi wannan kasar bashi wannan duk domin yaga mafarkinsa ya tabbata,itako Malika tatashi hannun Kafurai ne,bata taba zaton tana da Sirkin kamshin musulunci ba. Madam Dora ita ta sanyata amkaranta,kuma mkrantan ma,na Turawa,shiyasa tun malika na yar karama dabi'unta da kuma hallayanta yakoma na Turawa,domin a iya wannan Shekarun batataba sallah ba,domin madam dora bata koyamata ba toh masulmace ita,balle ta koyar da ita,wanda yakamata yazauna ya koyar da ita neman Duniya ya Rufemai ido,banda zuwa coci da karatun,bibble bata koyamata komai,domin tayi alqawarin bazata bar Diyar Juliyat ta subuce mata ba, ko kafin mahaifinta ya karbeta ta riga da ta gama tusamata duk wani akidansu. Shiko Abdulmalik duk wani soyayyah da tanadi wa malika yake yinshi domin yana matsanancin sonta da kuma tsausayinta na yarda bata taba shan Nonon uwa ba,sai dai madara,kuma bata rayu da mahaifiyarta ba,Shiyasa ya dauki son Duniya ya doramata yakan samu lokaci yazo,domin yanzu yabar england yana kasar spain yana aiki da wani kamfanin sarrafa agogon Fata na maza da mata,gida kuwa sai dai yayi musu sakon kudi ko ya kirasu ta waya bai samun sararin zuwa. Sai da aka kirasa aka sanar dashi Innaro ta rasu kana yaje Nageria lokacin kuma Malika tagama primary sch ,t yaso ya taho da ita,ammh madam Dora taki yarda ta dinga kawomai uzurin cewa Ga mkrantar ta,kar yatafi da ita karatun ta yatsaya,ita kuma bata so yatafi da ita ne yan"uwanshi su Farga Da Abunda ke Faruwa su riketa yaki dawo da ita,ta haka ta ribaceshi ya tafi ya barta,sai dai yaje ya sanar dasu da baki,babu wanda yanuna wani damuwa domin lokacin Abdulmalik shine Sarkin gidan sakamakon yana da kudi yanzu so babu mai ce mai baiyi Daidai ba. Bai dawo ba sai Da ya bada kudadade sosai wanda zai bude wani kamfanin sarrafa atamfofi akano,domin yanzu Abdulmalik yana da hannayen Jari da yawa akamfanoni da dama,shiyasa yake da kyakyawan alaka da Turawa sakamakon yasan harkan kasuwancin da yadda zai habaka kamfani ya shahara lokaci kadan ba"a Rufe Shekara ba *DAN KASUWA INVESTEMENT* ajahar kano, ya kammallah kuma kafin lokaci kadan ya shahara ako"ina aka sanshi kafin arufe shekara biyu Alhaji Abdulmalik ya mallaki manya kamfanoni masu yawa agida Nageria,kama daga na sarrafa takalma,dana Sarrfa kayan yara maza dana mata,harda na taliya,sai kuma na Tumatur,bayan gidajen man dayake dasu wanda ya bude su da sunan *MALIKA MALIK PETROLEUM NIG LIMITED* Ako wata wata jaha afalin Nageria in kaje zaka ga brach dinsu,hatta a malumfashi bai san iyakarsa ba. Bai tashi karban Malika ba sai da tagama Secondry sch dinta a england lokacin tana da shekara 18 Aduniya duk inda girma da budurci yake to Malika tagama mallakanshi,ammh kallon Farko zakayimata ka shaida da mahaifiyarta take kama,don tafi kama da baturiya Fiye da jinsu hausa Fulani,duk da baban inda yazo yana kokarin nusar da malika cewa itafa ba irin dangin mamanta bane ita musulmace,toh zata jishi ne kawai ko ya takuramata tayi sallah na ganin idonshi ne kawai yana tafiya zata watsar takama harkan gabanta,tun tana karama ta iya zuwa party da club clubs gashi ta koyo banzan dabi",an yayan Turawa na Shigar banza bata kunyar Fitar da tsiraicinta waje,gashi ,ammh wannan kwakwalwar ta mahaifinta tayi gadonshi wajen kokari da himma,Abunda yasa malika tadawo hannunshi saboda mutuwar madam Dora ce,yasa bayan anyi Shagalin binneta ya karbo malika tadawo hannunta wanda bai wani samu matsala da sauran yan"uwan mahaifiyarta ba,Tunda ya cikasu da kudi kuma yayi musu alqawarin kawota duk bayan wani Tsawon lokaci. A Canada Malika tahada digirinta na Farko akan Accounting daganan ta Wuce kasar America a babban birninta US tahada digirinta na biyu,bata dawo ba sai ta Hada takardan  Phd dinta,lokacin shekaru biyu da suka Wuce mahaifinta yagama cin moriyar Turawa suma sunci nashi yasa ya tararra yakoma gida akatsina ya gina wani tamfatsetsen gida mai kama da aljannar Duniya,kuma yayi aure da matarsa Hajiya Binta,yar"uwansa ce suka manna masa,saboda kudinsa,duk da ita Binta bata sonshi,dayake bazawarace,mijinta ya rasu ya barta da Diya daya mace JODA wacce bazata wuce Shekara 22 da biyu ba, ammh dole ta hakura Tunda kowa na Son daula ,uwa uba kuma tasamu jin dadin Rayuwa,domin shi ya kaita makka,kuma suna zuwa yawon duniya duk bayan wata daya bayan ya saka Joda a mkranta ,yanzu haka tana Final year dinta ne Barrau dikko dake zaria tana karantar SB NURSING. Tun zuwanta gidan Ta fahimci daga yar har uban babu mai tarbiya da ilimi gabadaya jahilci na dawainiya dasu ranar da suka fara kaima Malika ziyara a US sai da ta zubar da kwallah yadda ta ganta da irin Shigarta da yadda ta maida rayuwarta wlh ko wasu Turawan Sun fita kyan gani,gashi ya shagwabata ya sangarta baya iya mata Fada,yanzu sai takama kuka tana hargowa,shikuma baya son bacin ranta Shiyasa duk Abunda tagama dama shi takeyi,gashi Tun tana karama kudi sun batata komai take bukata aikwai Shi bata taba neman wani abu tarasa,tun dataji lbrin mahaifinta yayi aure,taji tsani matar tukan ta ganta,sai gashi sun hadu banda harara babu Abunda ya shiga tsakaninsu,sai ma ita Hajiya binta ne Alhaji Abdulmalik ya umarta data gaishe da ita Malikan saboda lalacewa,koda suka dawo gida,ta nemi gayamai gaskiya game da yadda yabari Rayuwar malika ta lalace tana ya"mace,ammh sai yaki bata dama yace ta kyaleta taji dadin Rayuwarta Allah yaba mahaifinta Dukiya mai yawa so Dole tayi Abunda taga dama.,Tundaga Ranar Hajiya binta takawo ido ta sanya musu bata kara saka Musu baki ba, Ba kome zasuyi tasani akwai ranar kin Dillanci. Bayan tagama karatunta dakyar Alhaji malik yashawo kan malika tadawo Nageria da zama saboda kula da kamfoninsa,saboda malika yarinyace mai kokari,she is very talent and smart,gata da wayau da kuma lura,shiyasa lokaci kadan Alhaji malik yasakarmata duka ragaman Kamfoninsa,domin ya Fahimci tafishi iya gudanar da komai,shi sai dai yana gida suyi waya agudanar da komai ita kuma malika taje ta tabbatar,kowani taro za',ayi,daga gida Nageria zuwa kasashen waje duk malika ke Zuwa ta gabatar da kowani ragama,shiyasa kafin lokaci kadan Tayi suna Aduniya don Aduniya inda kafarta bai taka ba kadan ne,kuma babu wanda baisan Rashin tarbiya da rashin mutumci irin na Diyar Abdulmalik Dankasuwa ba,abokansa sunsha zuwa suna kokarin mai nasiha ammh duk sai ya toshe kunni,daga kuma ranar ya yanke alaka da mutum,masu kwadayi kuwa sunsha kawo tallah da tushen hada ya'yansu aure da Malika ammh yaki bin mganarsu domin malika yanzu ba aure bane agabanta batama sanshi ba,domim bayan dawowarta dakyar da yaki yarabata da karatun Bibble,dakyar kuma ya ke sata tana sallah ammh wani lokacin,sai tazo kwanciya take hadawa,tana Tura bakin ita an takurata tafison Rayuwar england taje coci taje Club,tayi yawo yarda taga dama,ammh dawowarta Nageria,yasa duk tazama atakure ga wani takuran wai sai ta dinga sallah,ita wlh bazata iya ba,mganar dressing dinta kuwa Shi baya ganin aibun hakan,domin rashin saka dankwalinta yasamo nasabane da tashin datayi cikin Turawa shibaya ganin hakan awani mtsala Tunda shima ba ilimin addin yake dashi ba. Shiya samomata masu kula da ita mata har guda biyu mrry da Dose,sai excort dinta harsu ashirin masu take mata baya,in zata Fita kamar wata yar Shugaban kasa yadda combain yake biye da ita,ko kafin kace kwabo Alhaji Abdulmalik Dankasuwa yashahara kuma yayi Fice Aduniya bayan tarin dukiyan dayake dashi,ga kuma manyan hannayen jarin daya ke dashi akamfanonin kasashen ketare,inda malika take kula da Shige da Fitar komai,saboda hakanema yasa tayi karatu akan ilimin na"ura domin ta saukakama kanta wasu al"amuran rayuwa ta yau da kullun Tunda komai na business din mahaifinta ita ke kula dashi. Sau daya tataba zuwa malumfashi,ammh sai da tayi danasani saboda gabadaya garin bai mata ba,kama daga yadda aka dinga kallonta kamar anga wata bakuwar hallita,saboda yanayin shigarta uwa uba babu kallabi akanta sai gashinta data daureshi ta baya ta bazoshi,ba mutanen garin ba hatta dangin Abdulmalik ranar sunyi tir da Dabi'un Malika da suka mata mgana tayi musu Rashin mutumci ta zagesu tas tayi tahowarta,da suka kira mahaifinta suka sanar dashi sai ya goyi bayan yarsa yakuma ce ko suzo subata hakuri ko kuma ya cire hannunshi akansu,sanin da sukayi in ya cire hannunshi akansu sun bani sun lalace don basu da kamarsa yasa sukayi mota guda suka zo suka ba ma Malika hakuri wanda sai da baban yasa baki kana tace ta hakura,Tunda ga lokacin kowa yake kiyayewa saboda ita bata ganin kowa da daraja sai mahaifinta bandashi kowa zata iya takashi saboda kudi,tana ganin Duk wani mikamin Duniyan nan bashi da wani amfani in ba kudi ba. Malika ta zarce Duk Tunanin mai karatu ba yarinya bace shekaranta 27 Aduniya ammh in ka ganta sai kace yar Shakara 20 ce saboda yadda ta mori jiki,babu gidan Talabijin da gidan Jaridun da ba"ayi hira da ita ba,shiyasa sunanta yafi na mahaifinta shahara aduniya,malika ko abinci bataci da kanta bata akeyi ko wanka sai anyi mata saboda gata komai da kuka sani yimata ake,saboda tace matukar kudi na mganin komai to zasu mata mganin dukkan mtsalanta,Dawowarta Nageria basa ta rage zuwa clubs da party wani lokacin sai tsakiyar dare take dawowa  Akullum Alhaji Abdulmaleek Dankasuwa yana takaichin hallayar Malika musaaman ma n zuwa club da party,ammh bashi da yarda zaiyi da ita,don baya iya tsawarta mata ba, kana tana da wayau bata da yarda ko kadan,ko ma"aikatan ta da excort din ta bata yarda dasu ba,tana ankare dasu kuma tana bibiyan dukkan motsinsu. Abu dayane batayi Shine Zina,Malika bata yarda Akala tashiga tsakaninta dawani Namiji ba,sai dai in ta kasuwanci ko kuma abota,shima tun barowanta US rabonta da abota da Namiji,kuma tun alokacin ne da Sunan Abota take yarda tayi kiss da mutum sai dan Abunda ba"a rasa ba,ammh bata yarda wani yaketa mata budurci ba,saboda tana da bala"in wayon tsiya shiko mahaifinta tunda ya samu ya yakiceta da zuwa coci da karanta bible hankalinshi ya kwanta,sauran abubuwan datake kuma ko Abun na damunshi bai iya mata mgana Saboda yadda yake matukar sonta da kaunarta,so daya yataba kwantatan yimata Fadan ta rika sanya kayan hausawa,kuma ta dinga mutumta Hajiya binta, da malika tayi Fushi sai dai kawai yasamu waya kan cewa tana England takoma wajen dangin mamanta hankalinshi yatashi sai da yaje da kanshi dakyar da lallashi ta yarda zata dawo ammh da sharadin bazai kara takuramata ba,dole ya yarda da haka saboda yana Tsoron kada watarana Malika tayi Ridda takoma Kafura,duk ko ayanzu marabanta da kafurci ne kadan ne,banda sallah bata wani Abu na bautar Ubangijinta. itama sallar ba da kyau takeyi ba,ko Fatiha banajin tagama iyawa Saboda lalace babu Abunda tasaka agaba sai Duniya tanaYin duk Abunda tagama dama,ko dabi"ar Tubewa zindir wasu matan nayi miki wanka,Ai dabi"ar yayan Turawa ne wadanda basu san addini ba,ammah kome malika ta zama Aduniya sanadin yana wuyan mahaifinta domin Tun farkom gina Ginshikin samunta bai bi yarda Addinin mu ya tsara ba,koda aka umarceka ka auri Ahlul baiti bai chanchanci bayan haihuwar malika ya mikama Turawa rikon yarsa ba kuma yana sane da cewa sudin ba musulmai bane,taya zasu so malika ta koyi addininshi,shiyasa suka koyar da ita duk dabi"unsu da addininsu saboda ko gaba kada ta barsu. Ranar da suka hadu da Saleem har ta mareshi ta dawo Daga kaduna ne,wani party ne na ya"yan manya marasa jin mgana da"aka Shirya to daya daga cikinsu Friend dinta ne,Tun suna US shiya gayyaceta taje,shine da zasu dawo sukayi dare har su Saleem suka taremata motoci,Tun sadda Abun yafaru batakara Tuna wani hallita ba balle ta damu da Furucinsa na sai ya rama, ita tana ganin Shirmene da yarinta da kuma talauci da rashin nayi ke damunshi yasa,tun awajen ta tararrashi ta watsar ta cigaba da harkan gabanta,duk a iya tsawon wannan Shekarun babu Abunda ya ragu na Hallayar malika saima Abunda ya karu,Hajiya binta ko bacin kashin da bata gani har marinta malika tatabayi,ammh Alhaji malik bai dauki mataki ba,ita da banza Duk dayane,kallonsu kawai take tana jiyema Alhaji Ranar da zaiyi nadamar Turban daya dora Tilon yarsa akanshi. Tsakanin Malika da Joda ko basu da wani kyawawan alaqa,duk da ba sosai sukayi haduwa ba,wani lokacin in Malika na gida Malumfashi Joda ke Tafiya saboda ita yarinya ce mai hankali da gudun zuciya ga natsuwa,gata bata hayaniya,itakadai sai ta Shige daki tana kuka,in taga cin kashin da malika kema mahaifiyarta. Abun na damunta ammh bata da yarda zatayi sai hakuri saboda ko ita bata da bakin mgana, Saboda akwai lokacin da Makila tama Amminta rashin kunya,sao tayima malikan mgana,shikenan ta juyowa ta kasheta da mari,ta kuma sanya su Peter suka Dauketa chak suka Fita da ita daga gidan,tace kuma zamanta yakare agidan,sai dai Hajiya binta ta bita wajen tabata kudin mota tace ta tafi malumfashi Abun yamata bakinciki,sosai datatafi malumfashi tadade wajen Dangin babanta kafin ta dawo,shima saboda Ammin nata ne,ammh daga Alhaji Abdulmalik din har Malika ba wanda ya nemeta,sai ma goyon bayanta da yayi lokacin da hajiya binta ke sanar dashi Abunda tayima jodan,tabe baki yayi yace tayi Daidai Domin tana da iko da gidan Ubanta,Shiyasa Tundaga lokacin ta kiyayi kanta da malika. Iyakarta da malika sannu daga haka wata mgana batataba Shiga tsakaninsu ba,sai suyi kwanaki agidan ammh wlh ko zasu hadu sau goma ne ba wacce zatama wata mgana,ita malika tana ganin tafi karfin joda,saboda gidan mahaifinta take zaune,kuma take ci tasha tayi Sutura daga Dukiyar ubanta,to tana ganin tafi karfinta tsakaninta da ita kamar nisan kasa da sama, ne. Itako Joda tana kiyayewa ne Tun Abunda yafaru Amminta tajamata kunni sosai kan Malika,shiyasa tafita harkarta in taga damane ta gaisheta randa bata ra"ayi kuma tayi kamar bata ganta ba. *CIGABAN LABARI* _Washegari_ Saleem Tun bayan da suka dawo sallar Asuba da Abbi da ya marwan bai yarda ya kara haduwa dakowa ba,ko masallacin ana sallame sallah yayi Wuf ya Fito,saboda kada ya marwan ya tareshi da wata mgana,don bai shirya amsama kowa tambayanshi ahalin yanzu ba,sai ya aiwatar da gudirinsa akan Malika Yana dawowa ya Shirya domin komawa bakin aiki,ada yaso yabari sai gobe monday,ammh don gujema Fuskartar wasu barazanq mussaman ga Ya marwa da Ummi,shiyasa ya Shirya komawa batare da ya sanar da kowa ba. Karfe 7:00am na Safe ya Fito daga Dakinsa yana sanye da Uniform dinsa,sai wayarsa da makullin motarsa,Falon Tsit babu motsin kowa sai Ashura mai goge  goge ce kadai afalon tana share share,sama sama ya amsa gaisuwanta ya nufi koridon da zai sadashi da dakin Hajiya babba,domin itace kadai hope dinshi ayanzu. Koda ya Shiga dakin nata,tana zaune akan darduma tana laziminta na safe,domin a akidar hajiya in tayi sallar asuba bata tashi awajen sai  Rana ta Fito. Tana jin sallamarsa ta dago tana kallonsa,saboda yadda uniform din suka amsheshi ko ita sai da yayi ma kwarjini sosai,mirmishi ya sakarmata kafin ya karisa gabanta ya zauna bayan ya cire takalmansa daga bakin kofar dakin,yana Fadin"Hajiya barkanmu da Safiya..? Shafa addu"anta tayi kafin tace"Muntashi lafiya? sai ina naganga cikin Shiri kamar wanda akace gawani dan fashi chan? Dan mirmishi yayi kafin yace"Kaji hajiya,yo mu ai basai mun jira ance ga Dan fashi ba,mu da kanmu muke Fita nemansu,Tunda kinsan bazasu kawo kansu ba.." gyada kai tayi tana Fadin"Hakane kuma toh Allah yayi jagora.."Da Amin ya amsa kafin yace"Hajiya zan Wuce,nazo ne nayi miki tuni kan mganarmu ta jiya,wlh am serious don Allah ki matsama Abbi yaje yanemanin Aurenta plz.."Kai tsaye hajiya tace"Ina zanyi sanya,ai dolensa nema yaje,Abunda muke ta nema kuma Allah yakawo to me zamu jira?karka damu insha Allahu zaka aureta Tunda na lura kana sonta.." Dan cije baki yayi baiyi mgana ba,saima Kallon agogon fatan dake hannunsa yake,kafin ya mike yana Fadin"Zan Tafi hajiyata,nidai kiman kokari kome ke nan,zamu waya.."bata tashi ba tace"Toh Allah ya tsare..."Da Amin ya amsa kafin ya Fice. Daga Dakin Hajiya ko Dakinsa bai koma ba,yayi waje,motarsa ya Fada yamata key yana zuba hon,da hanzari maigadi yazo ya budemai get yana mai Fatan isa lafiya,babu wanda yasan Tafiyarshi agidan sai hajiya,shiyasa har sai da  akazo breafast ne,aka Farga saleem bashi agidan lokacin da Marwan ke tsiyan yasan Abunda yayi yaki Fitowa Hajiya ce tace",Wa..? Salihu ai ya dade da isa zamfara yanzu..."ba su kadai ba hatta da Ummi sai da Abun na Saleem yafara bata mamaki babu dai wanda yace kanzil kowa ya barsa da Abun Tunda ganin Shikanshi mai gidan bai ba mganar wani muhimmanci ba. shiko Abbi yaki bada Fuska ne saboda kada sumai wata mgana mussaman Ummi wacce Tun daren jiya taso tatadamai Tsiyarta yaki bata Fuskar yin hakan,data fara zencen ita bata yarda ba,kuma shima kada yabiyema Saleem,haryanzu yaro ne baisan inda ke mai ciwo ba,ammh ita bazata bari Akawo mata wannan Tsinanniyar yarinyar amtsayin Suruka ba ko alama.   Shikanshi Abbi ya Shiga dogon Tunani game da bukatar Saleem,duk shima yana da lbrin yarinyar kaf bamai dadi bane,toh ammh yayi Duba zuwa ga wani Abu,duk wanda yayi sanadiyar Shirriyan wani Shima yana da lada,sai dai kuma kafin ya je wajen Mahaifinta sai ya kira Saleem ya tabbatarmai ba saboda Dukiyan mahaifinta yakoson aurenta ba,duk yana da Shaida sosai kan tarbiyan ya"yansa,. Baya da Haufi kan Saleem domin yafi Shakuwa dashi fiye da marwan,wanda baima yi karatunsa a nageria ba,kuma yana da masaniyar Jarumi ne na karshe,wanda zai iya tankwasa ko wacce mace indai tana karkarshinsa ne,kuma aure ba haramun bane,sunnar ma"aiki ne kuma Dukkansu akanshi sukazo Duniya,shiyasa batare da shawara dakowa ba ya yanke zai kai ma Alhaji malik ziyaran Farko tun bayan kammallah jami"ar Dan Fodiyo basu kara samu zama sosai ba,sai dai haduwa sama sama,wanda bayan yazama IGP sun hadu sau biyu wajen taro wanda shima agayyaceshi ne yaje suka hadu,suka gaisa duk da kowa yana da nombar kowa,ammh basa mgana awaya,saboda yanayin aiyukan kowannensu.    _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 *JANAFTY* *💦MALIKA MALIK💦..!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *6* *Monday* monday Tushen aiki ko bature na tsoronta,Tun safe Abbi ya Shirya bai sanar da kowa ga inda zashi ba,ko Ummi bai sanar da ita ba,saboda tana Fushi dashi Tun safe ma ta Fice zuwa babbar kotun data ke aiki A higher suprime court Abuja. Karfe 10:00am na Safe suka dau hanyar katsina dagashi sai Direbanshi,Wanda marwan yaso ya tukosa,ammh ya dakatar dashi saboda bayason kowa yasan inda zashi. kokafin 12 da wani abu,suna kofar gidan Alhaji Abdulmalik Dankasuwa dasuka zuba hon cikin motarsa kirar vibe2k19,Da megadin ya leko sai da yatambayesu,ko suna da ganawa dashi Alhaji Abdulmalik din ne? amsa Abbi yabashi da cewa "A'a baisan da zuwanshi ba,ammh asanar dashi wani tsohon abokinsa ne daga gombe..."   Koda Alhaji Abdulmalik yaji  Haka Abun yabashi mamaki,don baitaba kawowa Cewa Kabir kumo bane,sai ya bada Umarnin abarsu su shigo,koda suka shigo cikin babban Falon gidanshi na kasa,aka sauke Abbi wanda yaji kayan alfarma kamar baza"a mutu ba,ko kafin kace kwabo ancika gabansa da kayan lashe lashe da shaye shaye. Yafi minti goma zaune kafin Alhaji Abdulmalik ya Shigo sanye da shadda gezner fara riga da wando,Abbi zaune yabama kofar Shigowa Falon daga cikin gida baya,shiyasa har Alhaji Abdulmalik ya kariso yana Fadin"Barka da zuwa..."   Juyowa Abbi yayi yana mirmishi yace"Yauwa...."Yafada yana mai kayatattacen mirmishi,Sake baki Alhaji Abdulmalik yayi,kafin ya rike bakinsa yana Fadin"Kabir kumo...? Yafada yana nuna shi,shima Abbi nunasa yayi yana Fadin"Na"am Abdulmalik Sa"ad.." yafada Fuskarsa da yalwa da Fara"a Rumgume juna sukayi suna mai murnan ganin juna kafin su saki juna mamaki bai bar Alhaji Abdulmalik ba,kara rike hannunsa yayi yana Fadin"Am very Suprise dana ganka agidana kabir,alhalin ni yakamata na fara kawomaka ziyara? garin yaya haka IGP guda yana yawo babu wasu masu tsoron lafiyanshi..? yafada yana dariya. Kafadansa Abbi yadaka yana Fadin"karka damu kanka Abdulmalik,gashi na nafara zuwa,mganar zuwa da Masu tsorona kuma,ni na dakatar dasu saboda bani son kowa yasan nazo ne,so nake ka ganni amtsayin Kabir kumo dina ba IGP Ba.."Dariya suka saka kafin su koma su zauna Alhaji Abdulmalik na Fadin"Am so happy wlh..Ya hanya..? Nan suka shiga gaisawa,sai kuma hirar yaushe gamo tatashi,dakuma tambayan iyalai,nan Abbi ke sanar dashi ya"yansa Uku maza biyu mace daya,Shikuma ya sanar dashi Yarsa dayace aduniyan nan,yana ta bashi kadan daga cikin nasarorin Daya samu atafiyar shi kasar England. Alhaji Abdulmalik dakanshi ya shiga cikin gida yakira Hajiya binta tazo suka gaisa da Abbi,wanda suka gaisa cikin sakin Fuska,kafin takoma ciki,nan da Alhaji Abdulmalik ya Umarci Da a shirya Abinci mai rai da lafiya ga Amininsa Kabir kumo,wanda suka baje suna ta hiran yaushe gamo,suna Tuna rayuwarsu ta mkranta suna Dariya Abun gwanin ban sha"awa. Malika bata Fito daga dakinta ba sai around 2 na rana koda ta Fito tana sanye da wani damammen wando pencil,wanda ya Fitar da duka suran cinyoyinta,rigar jikinta kuwa bata da hannu,wanda dakyar ta Rufemata cibi saboda rashin tsawo,kanta babu dankwali dama bata saba sawa ba,sai gashinta wanda ta daureshi daga tsakiya da band,ta saki jelan yana Mata yawo abayanta,Ear phone akunnenta wacce take jin waka da faskekiyar wayarta. Dakin Daddynta tashiga ta iske baya cike,da sassarfa ta sauko Falo tana kwalama Hajiya kira,tana kichen suna aiki da Atika,ta Fito tana amsawa karo sukaci da ita tana Fadin"Hajiya ina Daddyna..? na dubasa dakinsa baya ciki..? ta Fada tana Wani yamusta fuska,tana mele baki wanda yaji wani pick din jambaki. Kallonta tayi daga sama har kasa kafin ta kada kai tace"Yana Falon bakinsa na kasa,yayi bako ne.."kada kai Malika tayi batare datayi mgana ba Tanufi hanyar Falon tana tafe Gabadaya Hip dinta suna kadawa kamar wata karuwa baki Hajiya ta rike kafin ta bita da sauri ta rikota tana Fadin"A"a malika don Allah karki je ahaka kikoma ki Suturta jikinki don Allah..." Wani kallo tayi mata kafin ta waigo tana Fadin"Found of corection Hajiya,in Suturta jikina fa kika ce? yanzu ina yawo Tsirara ne..? tafada cikin mamaki tana bin kanta da kallo. Hajiya binta tayi saurin cewa"Bance kina tsiraraba,nufiba kije ki sanyo ko dogowar riga ki Rufe wannan kayan don Allah...",Tsaki malika taja tana Fadin",excuse me Hajiya.."Tafada tana zare hannunta dake kafandanta ta wuce tana wani kada kai kamar wata kadangaruwa. Fadowa kawai tayi Falon babu sallama,sai dai Alhaji Abdulmalik yaji kikam ta Fadomai ajiki ta Rumgumesa bayan ta sakarmai kiss agoshi tace"Daddylove i miss u..." Tunda Alhaji Abdulmalik yake da Malika bai taba jin kunyar Hallayarta da banzan Dabi"arta ba irin na yau,duk kunya Abbi ta kamasa,wanda yayi kasake yana binsu da kallon mamaki Mirmishin dole ya saki yana riko hannunta yace"Me too my Sweetbby,kin tashi lafiya..? baki tawani mele kafin tace"Fine Daddy..."Tafada tana kara gyara zama bisa cinyarsa idonta kur ana Abbi ammh baisa ta gaisheshi ba,duk ta ganeshi tana ganinshi albarai amtsayin IGP na Nageria gabadaya ammh ko agefen gyalenta,duk atunanin yazo maula ne wajen mahaifita tunda haka take kallon kowa. Alhaji Abdulmalik ne yace"Aermmm Sweetbby baki gaida bako na ba? Shima Abbanki ne,tsohon abokina ne,tare mukayi gwagwarmaya dashi a jami"ar Sokoto yanzu kuma Kinga yadda Allah ya maidashi shine inspector general of police na kasa gabadaya...",idonta kur akanshi kafin ta dauki Farin hannunta ta mikamai Tana Fadin"Hy...." Ai ba Abbi ba,har Alhaji Abdulmalik yaji ya muzanta da Abunda malika tayi kunyar Duniya duk ta kamashi,shiko Abbi mamaki tare da al"ajabi sun kamashi,lokaci guda kuma tsausayi suka bashi daga uban har yar domin zahirin gaskiya rayuwarsu na cikin tabewa. Mirmishi ya sakarmata bai mikamata hannun ba yace"kina lafiya...",Kai tadaga kafin tace"Fine....Same...."Tafada kafin ta mike tana Fadin"Daddynlove let me go, Zanje nayi breafsat sai ka shigo..."Dagahaka ta juya tana Tafiya Ko"ina na jikinta na rawa mussaman ma hip dinta,da hanzari Abbi ya kauda kai yana Ta'awizi aransa ayayinda Alhaji Abdulmalik ya sadda kai kasa yana jin wani iri aranshi. Abbi ne ya kaunda Shuru da jansa da wata hira shiyasa yadan saki sai da yaga haka kafin yace mai"Wannan itace malikar..? da kai ya amsa mai kafin yace"Yes itace,my dota ina alfahari da ita,domin acikin kaso mafi yawa daga Dukiyata samuwarta ya samo asali ne daga jajircewarta..."Jinjina kai Abbi yayi kafin yace",Gaskiya ne kenan ita ke Lura da komai yanzu,kai kana gida kenan.."Girgiza kai yayi kafin yace"Eh gaskiya kusan komai ita ke zuwa ta gabatar takuma tabbatar,wani lokacin sai akirani ta waya mu jadadda bayani,ammh gaskiya yanzu ragamar komai na hannunta don jiya tadawo daga london ma,kan mganar wani kamfani danike da hannu jari dasu.." Shuru Abbi yana jinjina kai kafin ya kalleshi kai tsaye yace"To kana shirin aurar da ita kuwa Abdulmalik...? Kuri yayimai da ido yana kallonsa gabansa na Faduwa,ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Ban taba sanar da wani wannan mganar ba sai kai kumo,wlh inason malika tayi aure saboda cikar mutucinta,ammh mtsala dayane Malika ,banta ganinta dawani Namiji da sunan suna soyayyah ba,kai infact ma nataba mata mganar aure nace yakamata tayi aure,sai ta sanar dani ita Batasan ma miye aure ba,ta,zauna karkashin wani ? to indai hakane har abada bazatayi aure ba,Abun na damuna sosai kumo narasa yadda zanyi ne.."Yafada muryansa ta chanza kamar yayi kuka. Riko hannunsa Abbi yayi yana Fadin"Meyasa? ai batafi karfinka ba,in ka Tursasa mata dolenta tabi Tunda kana matsayin mahaifinta,ammh cigaba da rayuwa haka Bazai yuyu ba,domin Duk ranar daka mutu wlh sai Allah tambayeka game da kiwon da kayima yarka.."Shuru yayi kafin yace"Bana iya Tursasa babby tayi abu,saboda ban son Abunda zai mata mata rai,zan dai gwada lallashinta,toh in ma ta yarda ina miji,nifa tsoro nakeji yanzu samarin zamanin nan duk ba don Allah suke aure ba,sai domin hannun jari,kuma samun Tsayayye jarumi wanda zai tankwasa Malika abu ne mai Wuya koni mahaifinta bana iya tankwasata toh balle wani.."Yafada cikin zafin rai,ashe Abun na damunsa bai iya Fadane. Ajiyar zuciya Abbi ya sauke aransa yana Fadin"An zo wajen..."gyara zama yayi kafin yace"indai wannan ne baka da damuwa,in ka yarda ina so zan neman ma Da'n wajena aurenta,i know My son very well zai iya Zama da ita harma daga karshe zamansu yabamu mamaki.."(Ya sanar dashi hakane saboda bayaso yace Saleem ne yace yana son Malikan,wanda dole zai zargi wani abu..) Kallonsa Alhaji Abdulmalik yayi bakinsa duka abude saboda Farinciki gefe daya kuma fargaba yakara damke hannunsa yana Fadin"Da gaske kake kumo..?,Gyada kai Abbi yayi kafin yace"Da gaske nake indai ka amince sai mai tattauna mganar..."Rumgumesa kawai Alhaji Abdulmalik yayi yanajin kamar yayi kwallah yace"Ngd ngd...Kabir kumo,hakika ba iya abota kakesona dashi ba,kai masoyin gaskiya ne,Tun lokacin muna mkranrta tare dakai,naji kunya lokacin da kaga irin rashin tarbiyan da Malika ta maka,ammh duk da haka bakaji komai ba,kakeson hadata da Danka wanda ko da banganshi ba,nasan yatara abubuwa dama kumo,sanin da nayi maka mai tarbiya da ilimi da hangen nesa nasani cewa bazaka bar zuru"arka haka,hakika kai abokina ne na nagari,ni kaina ina son Malika ta chanza kumo,ammh ya zanyi domin Na bar Shiri Tun rani,dana barta hannun dangin mahaifiyarta ta girma,duk shi yakara maidata haka.."Yafada yana sharbe kwallah kafin ya dago yana kallon Abbi. Mirmishi yayimai yana Fadin"Babu komai wlh,dama ita rayuwa haka tagada,ammh kaima danaga kuskuren data dawo wajenka bai kamata ka sakarmata ba Abdulmalik,ita Diya mace ba"a barinta haka ko Da namiji ya fandare balle mace,macen ma wacce ka sakarmata komai sai yadda tagama takeyi..."gyada kai yayi kafin yace"Ko baka Fada ba i know iz my mistake,bana bari wani ya sanar dani haka kabir saboda bani son Abunda zai dagamin hankali,kai ne mutum na farko dake sanar dani kai tsaye nayi ba daidai ba na gyara hakika nagodema Allah daya hadani dakai,yanzu kabar mganar komai ahannuna komai ke akwai zamu mganata ta waya buh yanzu in ka koma ka Turomin yaron wajen naka sai muyi mgana.. Hannun Abbi yabashi suka sarke yana Fadin"Masha Allahu,to ai bakomai zan sanar dashi insha Allahu..."Yafada yana bayyanar da murnansa,nan suka cigaba da tattauna al"amarin Alhaji Abdulmalik nata sanar dashi damuwarsa game da wasu dabi"un Malika bai iya boyemai komai ba,hatta ayadda abagaren addinin bata san komai ba,batayi iya komai na rayuwa ba,gazuwa club da Party ga rashin salla akan lokaci,Bata son komai sai rayuwar gata da jin dadi,yana Fadamai yana kwallah domin iya shekaru daya dauka da wannan takaichi bashi da wanda sai sanarmawa saboda duk Abunda malika tazama ayau Shine silan komai,Hakuri Abbi yayi tabashi yana sanar dashi insha Allahu zata gyaru. Sai gashi Abbi bai baro katsina ba sai da sukayi sallar la"asar kana suka dauko hanya kamar karsu rabu,hakika Alhaji Abdulmalik yaji dadin zuwa Abbi da duk abubuwan dasuka tattauna,yanzu Fargabansa daya da kuma Tunaninsa taya zai Tunkari malika da wannan mganar,domin yasani ko giyan wake yasha bai da ikon sanar da ita komai,gabadaya ya Shiga Rudani yakasa samun mafita,kuma bayaji zai iya hakura zuru"ar kabir kumo kamili da dattako ya Wuce Malika domin bayan shi din,ba uban da zaiji hallaya tare da Abun Tir game da malika kuma ya amince Dansa ya aureta,wannan sai uba na gari,da Amini na gari. Shiko Abbi har suka kai Abuja zuciyarsa na harbawa,yana so ya gano mai Saleem yagani wajen wannan yarinyar da zaice anema masa aurensa,shi dai bai hango wani quality wajenta ba,illah tarin munin dabi"unta,ada ya karaya ammh kuma sai ya duba da ya amince saleem ya auretama wani jihadi ne babba,toh ammh Abu daya yake son sani wani dalili ne ya sanya Saleem ke son aurenta? in har Abunda zuciyarsa ke zargi ne,to bazai lamunta ba,sai da ko yakira Alhaji Abdulmalik yabashi hakuri,ammh bazai yarda ayi Abunda daga baya zaiji kunya ba,da girmansa da komai..     ***************** Kwance yake akan makeken royal bed dinsa wanda yaji Shimfudun alfarma,katon bedroom ne mai dauke da gado,sai dressing mirror,sai wani katon wardrope wanda ya cinye rabin dakin akallon Farko zaka Fahimci ma mallakin dakin baison hayaniya da tarkace,domin daga kayansa dake sagale a hanger,sai jerin takalamsa kama daga sawu ciki,zuwa budaddu wanda suke jire bisa wani Stool mai Fadi da Tsawo. Dakin malale yake da wani Cafet mai taushi da Santsi bayan kuma daga Fentin dakin har kalan Funutures din ash and black ne.komai dai ya tsaru kamar ba dakin Namiji ba,saboda yadda komai yake atsare. Mamallakin Dakin yana kan gadon kwance dagashi sai bakin dogon wando,jikinsa babu Riga,gabadaya Fafaffadan kirjinsa wanda ke cike da gargasa,ya bayyana awaje,Mike yake sambal bayan duka idanuwansa suna sama suna kallon Rufin dakin,yayin da duka hannuwansa ya Sagale su abayan keyanshi yayi matashi dasu. yayi zurfi cikin Tunaninsa kafin karar wayarsa ya Dawo dashi,da hannu ya sa yajawo wayar wanda ke kan Stool din gadon,sunan daya gani ne yasashi sakin Siririn tsaki Afili ya Furta.."Kai Dis man,in maye ne in yakama mutum wlh sai ya ga bayansa haba.." Yafada irin Abun ya ishesa Din nan, dankawafar da wayar yayi yana tsaki bayan naga sunan mai kiran *FRIEND* ne da manyan baki,Idanuwansa ya kankance aransa yana Jin in ya hadu da saleema sai yaci ubanta,Bakin yarinyarnan kamar sikat,saboda rariya jikinta narawa komai akayi agida sai ta kira sadiq ta sanarmai kamar wata Sakarya,Abunda ya lura dashi daga shi har ita Tsofaffun munafukai. Tun jiya daya dawo Sadiq keta kiran wayarsa yana kin Dauka,domin yasan Tatsuniyar gizo bata wuce ta koki,Mganar malika ne yake so yamai,shikuma haryanzu bai shirya Amsa wata tambaya ba,ko kuma ya budi baki yayi bayani Abunda ke gabansa kawai Sai ya rama ne,shiyasa yake ganin kiran yana kin dauka. Wayar nasa ne takara dauka Tsuwa wannan karon dogon tsaki yaja ya mike daga kwance ya dauki wayar yayi niyyar ya dagane ya danna mai ashar sai yaga sunan Abbi na yawo asaman Sreen din wayar tasa,jikinsa na rawa ya daga kiran yana Fadin"Barka da Safiya Abbi.? Dagachan bangaren Abbi ya amsa da cewa"Lafiya lau Acp,ya aikin? ya karba da"Alhadulilallah Abbi ya gida dasu Ummi...? Abbi yace"Gida dukkansu suna lafiya,jiya kuma sai ka tafi ba sallama ko? Kunya takamasa sai ya kama sosa bayan keyanshi yana yar dariya yarasa tacewa,yar dariya Abbi yayi irin nasu na manya kafin yace"Mu bar wannan mganar,yanzu dai dalilin kiranka danayi dama juz na tambayeka tsakaninka ga Allah ne,Shin meye dalilinka nason Auren Diyar Alhaji Abdulmalik Dan kasuwa..? Gaban Saleem ya Fadi nan da nan zufa tashiga ketomai ta ko"ina azahirin gaskiya bazai iya sanar da Abbi dalilinsa na Son auren malika ba,kuma bazai iya sanar dashi don Allah yakeson aurenta,kada Allah yakamashi da laifin karya,gashi Abbi ya daureshi da cewa ya sanar dashi tsakaninsa da Allah. Kame kame yafarayi Muryansa na Rawa Abbi ya katsesa da cewa,"Kaga Ka natsu ni ba ina Turke ka bane naji dalilinka,ni Abu dayane nakeson ji,Allah yasa ba zargin danike akan ka bane,..? Saleem ya aro baki dakyar yace"Abbi wani zargi kake akaina..? Kai tsaye Abbi yace"Ina tsoron ko saboda kudin mahaifinta kakeson auren ta..?Ajiyar zuciya ta kwacema saleem ya saukarya yana jin wani sanyi aransa kai tsaye yace!Wlh Abbi Waye Allah..? shine Shugaban halittun duka Duniya ko? Toh Tallahi ba saboda kudin mahaifinta bane,haba Abbi kafi kowa saninmu,mu har wani kudi ne zai Rufemana ido,me muka nema muka rasa agidan Duniya.." Mirmishi Abbi ya saki kafin yace"Alhamdulillah,Naji dadin jin haka,dama Fargaba na daya kada wannan ne dalilinka daga baya azo ana jin kunya,Masha Allah jiya naje katsina na hadu da mahaifinta,dayake munada kyakyawan alaqa dashi na sanar dashi komai,kuma shima ya nuna murnansa kuma yayi na"am da mganarka.." Washe baki Saleem yayi kafin yace"Nagode Abbi Allah kara girma..."Abbi ya Murmusa yana Fadin"Ameen,ammh yanzu yace yana son ganinka,so in kasamu lokaci sai kaje ku gana ko? gyada kai yayi yana Fadin"To shikenan Abbi babu damuwa ko gobe ne sai naje ya ganni.."Abbi ya jinjina kai yana Fadin"To babu mtsala zan kirasa na sanar dashi zuwanka,kai kuma zan Turamaka nombarsa kaji ko.."Amsawa yayi da cewa,"Naji Abbi Allah ya biya bukata ngd sosai..."Daga haka sukayi sallama. Saleem ya tashi da sauri ya daka tsalle yana Fadin"Game din ya kusa karewa fa..."Malika malik ganin nan zuwa gareki.."Yafada yana wani Cije baki bayan ya datse lebenshi na kasa,yana wani juyi kamar wani zakin daya dade bai ga abinci ba. ___________________ Shiko Abbi koda yadawo koda wasa bai sanar da kowa Abunda yake Faruwa ba,kama bakinshi yayi ya tsuke yana jiran Saleem yaje katsina ya dawo komai kenan daga baya kowa yaji,ko Hajiya data matsamai sanar da ita yayi sunyi waya da Alhaji Abdulmalik ya sanar dashi baya gari ammh da zarar ya dawo zai sanar dashi,toh dahaka ya kashe bakin Hajiya. Itako Ummi bata kara marmarin karamai mganar ba,yasani ta sakamai ido ne taga iya gudun Ruwanshi,shiko yafi kowa karantarta tana da saukin kai,koman Turjiyanta kan Abu,da zarar ya tankwasata tana tankwasuwa,saboda yadda suke da Fahimtar juna,shiyasa bai damu da shariyanta ba,kuma mganar gaskiya duk wata uwa tagari bazata so Danta ya hada Zama ko Aure da Malika ba, domin kwata kwata bata cika sharudan zama mace tagari ba,Marwan ko Tun ranar litinin din yakoma,shi bai wani damu ba,don yana daukan mganar Saleem amatsayin Shirme ne kawai. Shiko Alhaji Abdulmalik Ranar bai iya Runtswa ba saboda damuwa da Tunanin mafita,duk Farkawar da Hajiya binta zatayi sai ta ganshi zaune ya jingina da gado idonshi biyu ya Shiga zurfin Tunani,in ta tambayeshi yace mata bakomai takoma ta kwanta Kawai,Farkawanta uku tana ganinshi cikin wannan Halin,Na karshen ne tatashi tashiga tiolet ta wanko Fuska tazo ta zauna kusa da kafafunsa tana Fadin"Haba Alhaji,wai meke Damunka ne,Tun dazu  dana farka sai na ganka zaune ka zabga Tagumi,kuma na tambayeka kace bakomai,Bakomai ne zaka kasa barci Fisabillah...? Tafada cikin kulawa Tana kallonsa,kur da ido,ajiyar zuciya ya sauke yana Sauko da kafafunsa kan lallausan Cafet din dake malale abedroom din,Dukar dakai yayi yana Jin Damuwa tayimai yawa,yana da bukatar Abokin shawara,Kuma yanzu bashi da kowa akusa dashi sai Binta,dalilin daya sanya ya dago yana kallonta kafin yace"Binta akaro na Farko Tun bayan aurenmu zan sanar dake damuwata ina Fatan zaki bani shawara don Allah..? Gyada mai kai tayi tana Fadin"insha Allahu Alhaji,dama amfanin zaman tare kenan..."Kada kai yayi kafin ya shiga zayyanamata yadda sukayi da IGO KUMO,har zuwa karshe ya karishe da Fadin"Ya kike ganin za"ayi Binta wlh ina tsoron sanar da Sweetbby wannan al"amarin bansan da wani Fuska zata kalli Abun ba infact ma ni banison Abunda zai bata ranta ,ammh mganar gaskiya inason Malika ta auri Dan wajen Kabir kumo,ko don samu ingantattacen tarbiyan dani mahaifinta na gaza bata..."Yafada cikin Raunin murya. Hajiya tayimai zuru tana kallonsa cike da mamaki kafin tace"Tabdijam babban mgana Alhaji,ammh azahirin gaskiya najima malika murna,domin ko ba komai Aure wani Nau"i ne na Bautan Ubangiji,da kuma Fatan Rabauta ranar gobe kiyama,ammh kuma wani hanzari ba gudu ba Alhaji a yadda ka bata yarinyarnan bana jin ko kai dakake mahaifinta zata saurareka balle kuma wani,..."Tafada tana jinjina Abun. Dafe kanshi yayi yana Fadin"Shine babban damuwana,Binta yanzu menene mafita..? Ajiyar zuciya ta saka kafin tace"Mafita dayane Alhaji,sai dai aboye wannan mganar kada asanar da malika sai bayan an daura auren kana,koda zatayi borinta na dan lokaci ne Tunda anrigaya da an Daura auren.." Kallonta yake yana jinjina kai alamun gamsuwa da shawaranta yace"Shawara mai kyau Binta,kinga yadda ma Tafiye Tafiyen kamfafoninnan suka gabato zata kashashe biyu ina jin kwanannan,Allah barshi sai ansanya lokacin bikin daidai lokacin da zata dawo..."Hajiya binta tace"hakan ma yayi Alhaji Allah dai ya Shigemana gaba...Da Ameen ya amsa kafin ya cigaba da sanar da ita sauran Shirinsa ammh zai ijeye komai sai yaron yazo su Tattauna. _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 09069067488 *SHAKIRA* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Masu tambayan *MALIKA MALIK* ko yakoma Free ne,No bai koma ba,yanan Ana saidawa kan Farashi mai sauki gamai bukatar Siyan Malik malik zai iya Turamin 200 kachal👌ta wannan account Nombar 0552179550,bayan kin Turonin hoton sreenshoot din payment din ta wannan nombar wayar 09069067488,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar wayar shima 09069067488,kai tsaye bayan an dauki hoton katin_ *Ina maraba daku masoyan gaskiya*😘 *7*    ""Washegari da misalin karfe 10 da wani Abu na Safe Saleem yadau hanyar katsina bayan ya kira Abbi yasanar dashi,shikuma yakira Alhaji Abdulmalik ya sanar dashi ga saleem nan zuwa. Shi ya tuka kansa,shiyasa  ya isa akan lokaci domin dama Saleem akwai gudu amota kamar zai tashi sama,koda ya shiga cikin garin katsina bai sha wahalan gane gidan ba,sakamakon gidan Alhaji Abdulmalik Dankasuwa ba boyayye bane a katsina,cikin lokaci sai ga motarsa ta tsaya abakin makeken gidan,wanda yake kama da wata al'karya guda. Hon ya zuba Kafin megadi ya leko yana Tambayansa sunansa kai tsaye yace"Saleem kabir kumo..."Bai yi watawata ba ya wangalemai kofar get din motarsa kirar 4matic ta sulala ciki domin dama Tuni an san da zuwanshi. Aparking space ya Faka motarsa kafin ya Fito yana bin haraban gidan da kallo,wanda wasu tafka tafka motoci iya kallon ka mallam,sukama gidan kwanya gefe daya kuma excorts din Malika keta zagaye suna wani Mazurai Dan ware ido yayi yana bin benen gidan da kallo yana jinjinama fasahar bazanin da maginin harda wanda aljihunsa yayi kuka,domin duk Abunda yake zato,toh ya ganshi Fiye da Tunaninsa. Komawa yayi ya jingina da motarsa Yana wasa da key din motarsa,sanye yake da Shadda mai Ruwan kasa wacce taji yarari da maiko,dinki tazarce ne yayi matukar amsansa,gefe daya kuma ya dora wata hula zanna bukar itama mai alaman zanen Ruwan kasa,hannunsa sanye da agogon Fata na kamfanin Rado,shima mai kalan Ruwan kasa,bayan takalminsa shima Rufaffafe ne na Fatar damisa,shima kalan Ruwan kasa,kallo daya zakamai kaji kakasa kara kallonsa saboda yadda kwarjinsa da haibansa ke tasiri a idon wanda ya kallesa mace kuwa komin Girmanta da ajinta,da isarta da takamarta da duk Abunda take takama dashi,in ta kalli saleem sai taji ta raina kanta da duk Abunda ta mallaka. Bai Dade da tsayuwa ba,yaji muryan wata mace cikin hadadden Turanci wanda dagajinsa kasan mutum ba haye yayi ba,ya kware ne,daga gefensa kamar bazai daga  kai ba,sai yadaga idonsa ya Fada kan Malika wacce ke Tahowa daga bayan gidan Daga ita sai wani karamin mini sikat,da wata riga kai breziya ce ma,domin banda kokon nono bata tare komai ba gashin kanta ajike yake da karamin Towel akanta tana gogewa da hannu daya,dayan hannu kuma tana mgana awaya,fararen kafafunta da cinyoyinta awaje suna kyalli,bayan kafarta na sanye da wani Takami flat mai taushi. Bayanta Merry ne da Dose,merry na Rike da robar Ruwansha,ita kuma Dose tana rike da wani karamin Towel din,dukkansu suna biye da ita kamar rakumi da akala,bai gama mamaki ba sai da yaga tabiyo ta gabanshi cikin wannan banzar Shiga ko ajikinta ta kuma ratsa ma,'aikatan gidan,wadanda suka kame mata kamar wata matar Shugaban kasa,Bayanta yabi da kallon Tir,yana jin wani takaichi aransa ganin yadda gabadaya idon kardawan arnan samudawan ke kan Hips dinta wanda ke Juyawa kamar wanda ake controle dinsu. Saurin Kauda kai yayi yana kiran Sunan Allah,wani Siririn tsaki yaja yana Fadin"Lalle yarinyarnan ta Wuce da Tunanina,ashe tsinanniyace ta karshe bansani ba....'Yafada yana rike haba,yana bin Kofar data bi da kallo,Bai gama mamaki ba,sai ga Alhaji Abdulmalik ya Fito da hanzari cikin Fararen kaya yana saba babban Riga ya kariso wajen Saleem yana Fadin"Am srry na barka awaje ko..? Yafada yana kokarin mikasa hannu ammh sai Saleem yaki bashi hannu sai ya rankwafa yana Fadin"Ina Wuni Daddy..."Yafada yana sadda kai,Dagosa Daddy yayi yana Fadin"Ash Tashi Tashi mana,Saleem ko..',?Yafada cikin Fara"a, Gyada kai Saleem yayi yana Sadda kai,kafadansa Ya kama yana Fadin"Masha Allah..."Yana kallonsa murna da Farinciki sun cikashi ganin Saleem amtsayin Surikinsa koshi dayake Namiji kwarjinsa ya dakesa sosai,Yana Rike dashi Har zuwa Babban Falonshi na saukan baki,ya zaunar dashi bisa kujera,wanda Saleem din yayi saurin zamowa kasa yana dukar dakai. Yar Dariya Daddy yayi yana Fadin"A"a Haba Saleem,maza tashi ka zauna da kyau nan ma fa gidanku ne,nima Abbanka ne ko Kumo bai sanar dakai bane..?"Yana duke ya murmusa yana Fadin"Ya sanar dani Daddy kayi hakuri kabarni anan..."Dariyan Farinciki Daddy yayi yana Fadin"Toh indai ka dauke ni a mtsayin Daddynka toh na baka Umarnin katashi ka koma bisa kujera kaji.."ba yadda ya iya,sai tashi ya koma bisa kujeran yana Kallon Cafet din daya karama Falon kyau. Kallonsa Daddy yake ransa na Fari,Aransa yana ta Fadin masha Allah,waya ya daga ya kira Hajiya binta yace akawoma Bako Ruwa da lemo,ai ba'a dauki muntuna ba,sai ga Atika da Tire niki niki da lemuka da Ruwa ta ijiye gaban Saleem bayan ta duka ta gaisheshi,ya amsa bai kalli ma inda take ba idonsa na kasa. Mikewa Daddy yayi yana Fadin"Bari na barka kasha Ruwa ka huta kafin nazo muyi mgana ko..? Mirmishi Saleem yayi baice komai ba har Dadddy ya Fice daga Falon jikinsa na rawa,Da kallo mai kama da harara Saleem ya bisa kafin ya saka hannu ya dauki Ruwan swan ya tsiyaya akofi yasha,Ajiyewa yayi yana sakin ajiyar zuciya Lokaci daya yana bin Falon da kallo Yana mele baki Bai jima ba,sai ga Daddy ya dawo yana ganinsa yayi kasa da kai kamar wani na gari,nan ko zaginsa kawai yake aransa,domin hardashi abada Gudummuwar Wulakancin da Malika tayimai,kusa dashi Daddy ya zauna yana Dafa kafadansa kai tsaye yace"Sannu da zuwa,hop kazo lafiya..? Saleem ya amsa da cewa"Alhamdulillah.."Alhaji Abdulmalik yace"Masha Allah nasan dai mahaifinka ya sanar dakai komai ko..",?Gyada mai kai kawai Saleem yayi,kafin ya cigaba da Fadin"Toh naji dadin hakan,yanzu Abunda nakeso dakai kamar yaushe ne kake bukatar ayi auren ...? Saleem yaji ransa Fes,ammh sai ya basar yana Kara sadda kai yace"Daddy duk yadda kuka tsara ni awajena Daidai ne.."girgizamai kai Daddy yayi kafin yace"A"a ba ahaka Saleem ai kaine zaka zauna da ita,kai ya kamata ka sanar damu zuwa yaushe kakeson ayi komai agama.."Shuru yayi kafin yace"nan da Wata daya yayi Ko...,? Daddy yace"Yayi sosai ma,Allah ya nunamana yanzu kana wani aiki ne...? Saleem yace"Ina aiki a zamfara ne,karkashin wata headquter,a mtsayin Acp..."Washe baki Daddy yayi yana buga kafadansa yake Fadin"Wow Bravo...Ashe magajinn kumo ne,gaskiya am so happy to hear dat,Allah ya taimaka.."Yana mirmishi ya amsa da Ameen. Gyara zama yayi yana Fadin"Kana da muhallin ma"ana wajen da zaku zauna...? gyada kai Saleem yayi kafin yace"Eh inada dan madaidaicin gida anan zamfaran..."Shuru Daddy yayi kafin yace"Toh babu laifi,ammh akwai Abunda nakeso na sanar dakai,bawai don zaka auri yata ba A"a don kaima kana mtsayin Dana ne ko ba malika zaka aura ba,zan maka dukkan Abunda yakamata.." Saleem ya jinjina kai yana Fadin"Hakane Daddy..."Yace "Toh Abu na Farko Shine bani son ka kashe sisinka amganar auren nan bayan sadaki,duk wani Abun bukata,kama daga lefe da gidan da zaku zauna duk zan tanadar muku kaji.."Mirmishi Saleem yayi kafin yace"Ayi haka Daddy...'Kafadansa ya dafa yana Fadin"Karka damu Dukkanku ya"ya ne,so yanzu sauran mganr zamu tattauna da mahaifinka kaji ko,Allah yayi maka albarka yakuma baku zaman lafiya.."Afili ya amsa da Ameen ammh cikin ransa ba Ameen ba yake fadi ba,yana ayyana yadda rayuwarsa zata Cutu matukar Allah yabasu zaman lafiya da wanchan tantiriyar yar iskan. Mikewa Daddy yayi yana Fadin"Yanzu zaka Wuce ne,ko akirama ita ku gaisa ne?."(Shima dai kawai ya Fadane kada Saleem din yagano ita malikar bata sani ba...) Saurin Girgiza kai saleem yayi yana mikewa yace"A"a Daddy rabu da ita,zan dawo insha Allahu,yanzu ma ina Sauri ne aiki yayiman yawa a office ni zan koma..."Daddy yace"Haba ka tsaya kayi lunch mana!Saurin girgiza kai yayi yana Fadin"ngd daddy..." Bai hanashi ba illah Shiga ciki dayayi ya kira Hajiya binta suka gaisa,wanda itama ta yaba da Saleem din,kuma aranta tana ganin Malika ta samu daidai da ita,har bakin mota Daddy ya rakasa yabashi rafar kudi yan Dubu ammh Saleem yaki karba sai da yaga ya nuna baiji dadi ba kana ya karba,har ya Fice daga gidan yana dagamai hannu da Fatan Allah ya kaishi lafiya. Saleem na tuki yana cin dariyan Ladabin karyan dayayima su Alhaji Abdulmalik,domin harga Allah baya wani ganin mutumcinsa,kawai yana mai na yan Duniya ne,ammh ina Abun girmawa anan wajen,yana babba ammh sam baida Tunani yabar yarinya na Abunda taga dama,ammh no wahala karshenta ya kusa zuwa,domin dama yace wata daya ne don ayi komai a Wuce wajen,Yaci burin yadda Adare daya malika ta chanzamai rayuwa,shima yayi al"kwarin chanzamata shi awannin goma ne bama sai an kai ga cikar dare ba,kudin daya bashi yake kallo yana harara,yana fadi afili,"Dole mana kabani kudi,Tunda za"a Tusa min Ragowar arna,yaga yaro shar zai makalamin tsohuwa,yo tsohuwa man wanda naba shekara daya,ai ta tsufa..."yafada yana sakin tsaki yana cigaba da hararan kudin kamar sune Alhaji Abdulmalik din.    ***************** Saleem bai kira Abbi ya sanar dashi Abunda ya wakana tsakaninshi da Alhaji Abdulmalik dan kasuwa ba,shi da kanshi ya kira Abbi ya sanar dashi komai kuma yana kara yabawa da Saleem din,Ada Abbi yaso yayi Turjiya game da Cewar dayayi sadaki kadai yake bukata,ammh sai shi Alhaji Abdulmalik Dankasuwa ya nuna daga Saleem din har Malika shi uba yake garesu,saboda yana da hakkin yimusu dukkan Abunda ya kamata,nan yake sanar dashi ya tsaida mganar auren nan da wata daya,. Abbi yaji dadin karamcin Alhaji Abdulmalik har ya nuna yana so yan"uwanshi baffanninshi da suka rage akumo zasu agabatar da neman aure,Alhaji Abdulmalik ya dakatar dashi da cewa basai sun zo ba ai duk Abun na gida ne,su bari Ranar daurin Aure sai suzo tare da Sadaki,babu komai shi ya riga yaba saleem malika har Abada,da wannan mganar sukayi sallama cike da Farinciki. Abbi baya da zabi illah sanar dasu Ummi halin da'a ake ciki,wanda Hajiya ce kadai ta nuna murnanta Afili ,ammh Saleema da Ummi Kamar su fasa ihu saboda bakinciki,Saleema ta bude baki tana Fadin"Haba Abbi yanzu Fisabillahi in yaya Saleem baida hankali da Tunani sai ka biyemai,yanzu don Allah duk matan Duniya yarasa wazai aura sai Wannan yar iskar...? Tafada idonta cike da kwallah,hararanta Abbi yayi yana Fadin"Kul na sakejin kina kiranta yar iska,iskancin me tayi miki toh zan sabama miki wlh in bazakima dan"uwanki Fatan alheri ba juz keep ur mouth shout tunkafin na saba miki wawiya kawai...",Yafada cikin Fushi. Saurin mikewa tayi tana kuka ta Wuce zuwa dakinta,Ummi dake zaune batace komai ba,Hajiya ce ta kalli Abbi tana Fadin"Wai ni kabiru Meye dalilin da yaran nan basu son Auren nan,kodai ba diyar kirki bane...? Ummi tayi Saurin taran hajiya tana Fadin"Wlh bs diyar kwarai bace Hajiya,Yarinyar kwata kwata batayi kama da..." "Aisha....."Abbi ya katseta da tsawa yana kallonta,shuru tayi da bakinta tana Jin wani daci aranta,Bai kara mgana ba ya tashi ya haye sama ammh daga yanayin kallon da yayimata Jikinta yayi sanyi,tashi tayi tabi bayanshi batare data kara cema hajiya komai ba,. Hajiya tabe baki tayi ta mike tana Fadin"Allah ya kyauta..."Daga haka ta shige dakinta Ranta fes Domin Dama babban burinta shine su Saleem suyi aure tagaji da ganinsu haka ba iyalai. Shiko Abbi yana Shiga daki sai ga Ummi ta biyo bayansa tana Shigowa ya tasomata yana Fadin"Haba Aisha meyasa kike haka? ke yanzu Abunda kikayi Yayi kama da Abunda uwa tagari zata aikata,kada kimanta kema kinada Diya mace,in aka aibatata zaki ji dadi? kada ki manta Allah shi ke shirya wanda yaso ya batar da wanda yaso,nasan kuma kina da sani kan hakan bayan karatunki na Shari"a low kina da karatun Addini daidai gwargwardo,why kika aikata haka? Yafada yana kallonta kur da ido ganin yadda jikinta yayi sanyi ne yasa ya juyamata baya yana Fadin"Kin bani mamaki Aisha,wlh ayadda na sanki mai hankali da hangen nesa banzata zaki ki bada goyon bayan Saleem yayi jihadi ba,baki Tunanin in ya aureta ya natsarta da ita,dani da ke dukkanmu munada lada? Gaskiya ban zan boye miki ba u already disoppoiting me Aisha..." Yafada Yana jadda  kalamansa,Kukane ya kwacemata ta isa gareshi ta rumgumosa tana Fadin"Kayi hakuri yallabai,wlh nakasa sarrafa zuciyata ne na ganin Saleem ya auri yarinyar nan, da Duniya tagama saninta afannin rashin tarbiya da kamewa mezan cema yan'uwana da kawayena? wlh Abun kunya ne babban Amtsayinka na mai mutunci aji mun hada zuru"a dasu,sai ma afara zargin kila kwadayin Dukiyar mahaifinta ne ya Tsolemana ido... Tana Fada tana Sheshshekan kuka waigowa yayi yana rikota gefen gado ya zaunar da ita yana Fadin"kalle ni nan Aisha.."kai tsaye ta dago tana kallonsa hannunsa ya mikamata ta kama kafin yace"Tun sanda kika zamo mata nake mika miki hannuwa na domin ki kama,yazama bango da majingini gareki,kuma har gobe zan cigaba da mikamiki ,Toh yau gashi na kara mika ,mi ki ki kama ki damke yazama kariyarki har gobe kiyama ki kuma saka aranki indai Dan dani Kabir na haifa tare da Aisha ne bazai zamo gafalalle ba,sai da ikon Allah,na yarda da zencenki na za"a ce ko muna hangen Dukiyar mahaifinta ne,yes Alhaji Abdulmalik yana da tarin Dukiyar da baisan yawanta da karshenta ba,ammh wlh tallahi Aisha Dukiyarsa bata taba tsolenmun ido ba,mena nema na rasa,akwai Abunda bazan iya mallaka bane anan Duniyan...?Babu shi to kisa aranki Da zuciya daya na yarda da wannan auren,ki kuma toshe kunnuwanki daga zencen mutane,dama wasunsu dayawa basu son akullah alheri,ki kuma yi kyakyawan zato ga Danki,kinsan Abunda zai aikata da wanda bazai aikata ba,don Allah ki Cire wannan Tunanin azuciyarki kisama auren nan albarka kuma ki Rufe kofar da wani zai kawo kushen wannan Auren don Allah....," Yafada yana kara damke hannunta hawaye ne suke shatatamata kawai sai tafada kan kafadansa tana Fadin"Na yarda kuma na saka musu albarka...Allah ya sanya alheri,ka yafemin yallabai,Akullum ina alfahari da samun miji gwarzo kamar ka,lokacin da na nemi kauce hanya sai kayi saurin dawo dani,Allah yabani ikon Yima biyayyah har karshen Numfashina,Allah kuma ya Shiryamana Zuru"a...."Da Ameen yayi ta karba bayan ya sanya hannu yana Sharemata hawaye yake Fadin "Toh bar kukan hakan,Fushi ya kare ko..."Yafada yana dariya Kirjinsa ta fada tana Rufe fuska wai ita kunya,yar dariya yayi yana Fadin"A'eesh dita har gobe bani da kamar ki AISHATUL HUMAIRA..."Yafada yana Mata rada akunne,Rumgumeshi tayi itama tana mai rada akunni,nidai nayi waje Tunda dai naga ma"auranta sun daidata kansu dole na ja Siraran kafafuna zuwa waje😂 ___________\_________ Tundaga Ranar Ummi ta fauwalama Allah komai ta karbi Auren saleem da hannu biyu,wanda harshi sai da takira tana mai Tsiyan yana Fushi da ita kwaso rantsuwa yayi yana bata hakuri,dariya kawai tayi tana sanyama auren albarka,aransa bai amsa da Ameen ba,don cewa yayi ai dama baki sakko ba Ummi,don ba auren gaske bane,na Ramuwa ne kawai na awannin kadan,ammh duk da haka bata makara ba😂 Saleema ko kwana uku takara takoma mkranta bayan taga gidan gabadaya anhada kai babu mai goyon bayanta,Ummi ce toh itama yanzu tabi bayan mijinta,Hajiya kuwa batama sauraran mutum indai ta Fahimci zai kawo wata sukane game da auren Saleem,shiyasa ta tattarara kayanta Takoma mkranta,kuma tayi alqawarin ko bikin yatashi wlh bazata zo ba,indai da wannan Jinin Turawan ne. Ita ta kira ya marwan ta sanar dashi,wanda yaji Abun kamar almara,nan da nan ya hau Shafin instergram,ya bude shafin Malik malik,nan yaga badala kala kala nata,Tunda abokan aikinsa sunsha Tuka jirgin data ke ciki ita da Amintattun Escorts dinta,ammh shi bai taba katari da shegiya ba,duk da yasan lbrinta ba boyayyiya bace,anan nema yake ganin Jiya da misalin karfe 2:00pm jirgin daya tashi daga Abuja zuwa Amurka tana ciki wai tatafi tarin karama yan kasuwa sani da Duniya gabadaya ta Shirya akasar ta Amurka,irin hotunan data daura da shigarta Abun ba kyan gani,nan da nan zuciya ta debi Marwan ya daga waya ya kira Ummi yana Kumfan baki tana gani Saleem zai auri wannan Shegiyar yar iskan yarinyar.? Ashe Abbi na kusa yako karbi wayar yayima Marwan din Fata fata daga karshe ya bishi da Nasiha mai kashe jiki,shima din jikinsa yayi sanyi Domin yasani Shi da Allah ya Shiryar dashi bayafi sonshi bane,haka Allah yake Abunshi shi zai raya wanda yaso,kuma ya kashe wanda yaso,shi zai Shiryar da wanda yaso,Allah shike da ikon Umartan Faruwan Abu nan take kuma ya Faru ko ya kasance,ya sanar dashi ko ya manta kissan Annabin Allah Annabi Yunus wanda yayi Fushi da mutanensa ya baro garinsu zaiyi hijira ya Shiga jirgi sai aka ga jirgi na tangal tangal,nan masu jirgin sukace akwai wanda yayima Allah laifi acikin Jirgin,nan suka ganoshi suka jefasa cikin kogin,shikuma Allah nan da nan ya Umarci Kifi data hadiyeshi,ya sanar dashi Allah yace acikin alqur"ani mai girma ba domin Annabi Yunus yanemi gafarar Allah ba da ya dauwama acikin cikin kifin nan har ranar tashin kiyama. Hakuri yayi ta bama Abbi,domin Hakika duk Abunda ya Fada gaskiya ne, domin sau nawa zamu dunga aibata yan"uwanmu da jifansu da  munanan kalamai a maimakon murika musu Fatan Shiriya tunda munsan babu mai batarwa,kuma ya Shiryar sai Allah,kuma hadisi ne ingantattace sau tari Mutum zai Fara aiki irin na yan Aljannah sai yana gabda mutuwa aikinsa ya juye yakoma na yan Wuta kuma ya mutu ya shiga Wutan,ALLAH YA KAREMU...Kuma sau tarin mutum yana ta aiki irin nan yan Wuta kwatsam sai yakoma aikin yan aljannah,kuma ya mutu alokacin ,sai kuma ya Shiga Aljnanah,to mai zamu ce da haka? musani Aibata wani mumina ba dabi"a mai kyau bane.domin babu wanda yasan tsakanin Ubangiji da bawansa... _Allah ka shiryemu kabamu ikon sarrafa zuciyarmu ta hanyar mai kyau_ _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 *Shakira* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *8*   "Yana zaune cikin Office dinsa aiki ya kacame mai Sargent musa ya shigo agabansa ya tsaya hannunsa asaman kansa yana Fadin"Weldone sir...." Bai dago ba ya amsa da cewa"Weldon..Arm ya"aka yi ne Sargent musa..? Baya yaja yana Fadin"Yallabai kayi bako ne,yana waje yana son ganinka,ya shigo ne..?"Shuru yayi kafin ya dago yana Fadin"Bako kuma? Who...? Sargent musa yace" I don"t know sir buh kamar naga na gida ne"Tsaki yaja kafin yace"Let him in,buh dagashi bazan kara ganin kowa ba gaskiya a hv alot to do,koda wani ne yazo yana son ganina matukar iz not imfortant,plz tell dem bani nan ok..."saramai yayi kafin yace "Yes Sir..." Ya Fice da Hanzari,shiko yamaida hankalinsa kan karamar syestem din dake gabansa wanda da alamu dai Abunda yake yaja ra"ayinsa. Sargent musa bai dade da Fita ya Turo kofar office din ya Shigo yana kwarara sallama."Assalamu Alaika..."Aka Fada ana yar dariya,Dago kansa yayi ya Jefa cikin na mai sallaman,kai tsaye bayan ya dauki hannunsa wanda ke rike da pen yana sosa gemunsa dashi yana kara kallonsa kasa kasa,shiko Sadiq dariya Abun ya bashi ammh sai ya doje, ya karisa yana Fadin "Haba Friend kuma shikenan don kazama Mijin hajiya sai azubamu akwandon shara,kuma ma don katon Wulakanci bayan Rejecting din call dina dakakeyi na baro uzirin gabana nazo inda kake ba mirmishin maraba balle abani wajen zama, ko..? Yafada yana zama cikin daya daga cikin kujerun da suke Fuskar Saleem din. Wani bad look yamasa kafin yace"Ammh wlh kai kam indai aka leqa Wuta baka to kila ka makaleni,😝gulma da munafunci suna cin gindinka shege Bawan mata kawai..."Dariya Sadiq ya sheke dashi yana Fadin"Uhum sai ba kai ba,wai meyasa kasama rayuwata ido ne,badama nayi magana sai kace na cika gulma,kuma in an bibiya wlh gaskiya nake Fada.."Yafada yana kara saka dariya, Tsaki Saleem yaja kafin ya tashi ya isa ga karamin Frigde din dake office din ya dauko Ruwa mai sanyi yazo ya ijiye agaban Sadiq,yana mai zama kujerar dake kusa dashi yake Fadin"Naji mallam,yanzu dai lafiya Tunda ga Abia ka bugo sammako,ko kana  bina bashi ne...? yafada Fuska Daure,dariya Sadiq yayi kafin ya dauki Ruwan daya ijiyemai ya bude ya kurba kadan kafin ya ijiye yana Fadin. "Nazo yimaKa Allah sanya alheri ne,naji Abun alheri,ance ma ansaka ranar aurenka kai da Diyar Dankasuwan nan Alhaji Abdulmalik,wama take da suna...? Yafada yana Rike haba,kuri Saleem yamasa da ido kafin yace"Ok nagode yaushe kazo garin..? ya fada yana basar da zencen,Shiko Sadiq ya gyara zama yana Fadin"Jiya na iso,kuma yau nace kai zan dakama sakkko naji dadin ratayeni dakayi baka daga kirana,ko kafarama irinmu nisa ne Tun yanzu..."Mirmishi Saleem ya saki kafin yace"Eh duk yadda ka dauka hakane,ya aikin..? Sadiq yace"Normal,ya shirye shirye...? tabe baki Saleem yayi kafin ya mike yana Fadin"Babu wani Shirye shirye daga wajena kabaro wajen da"ake Shirya komai ma"ana gidan Abbi..."Dariya Sadiq yayi kafin yace"Friend nazo ne muyi Serious tok dakai,wai don Allah meye ka gani jikin wannan watsatsiyar yarinyar da har ka makale sai ka aureta...? yafada Shima Fuskarsa nasa na rage Fara"a,ko kallonsa Saleem bai yi ba yace"Me ruwanka Allah yasa Tambadaddiyace ba watsatsiya ba,ni naji na gani,so plz and plz Sadiq stay out indai akan wannan mgananr ne, matukar kanason mu cigaba da zama a mtsayin abokai...",Yafada babu wasa amganarsa. Baki Sadiq ya rike yana Fadin"Haba Friend ina laifi don na gaya maka gaskiya,karka manta Ance mu zabama ya"yayenmu uwa tagari...."Cikin hargowa Da Fushi Saleem yace"Plz Sadiq i said stay out of it ko? kada ka Tunzarani nayi Abunda banyi niyya ba"Yafada idonsa yakada yayi jajir,kuma muryansa a kausashe,Shuru Sadiq yayi yana kallonsa kafin yayi ajiyar zuciya yana Fadin"Is ok,yanzu meye Shirinka akan shagalin bikin,bawani event ne,ko daga bangaren Amaryan...? Saleem yayi kasake aransa yana Fadin"Kai Sadiq maye ne wlh,...? Fuska ba Annuri yace"Nifa ka ganni nan babu Abunda zanyi ko gayyata babu wanda nabashi aikin balle yazo ya wahala Saboda ni kai infact ma ni banda ku na gida babu wanda zai san da wannan auren nan,so plz mu chan wata hirar.."Yafada yana zama bisa kujeransa Fuskarsa kuma taki bada dama balle har Sadiq ya Fahimci wani Abu. Duk yadda yaso ya bugi cikin saleem shiko yaki bashi dama,dole ya hakura suka shiga wata hirar,sai wajen la"asar kana yayi mishi sallama yakoma Abuja,bayan sun rabu kan gobe zai koma bakin aiki sai kuma Lokacin bikin na saleem in ya samu dama zaizo Daurin aure,shiko saleem yana mirmishi yacemai in bai samu lokaci ba kada ya takura kanshi,Abun yabama Sadiq mamaki,nan da nan kwalkwalrsa tashiga Tunanin akwai lauje cikin nadi,game da wannan auren na Saleem,ammh duk da haka zai cigaba da bibiyan al"amarin har ya gano gaskiya duk da Shi saleem din ya ki bashin damar Fahimtar hakan.   _____________________ *BAYAN SATI BIYU* Shirye shirye ta ko"ina ya kamkama,Abbi da kansa ya kira mutanen Kumo ya sanar dasu,tare kuma da sanar dasu lokacin biki,Hakama Ummi ta sanarma duk wanda yakamata yaji,ammh bata bada Fuskar wata mgana ta shigo ba,duk ba kasafai take iya sanar da wacece Shi Saleem din zau aura ba.daga ita har Abbi suna ta gayyan mutane da yan"uwa da Abokan arzuka ayayinda da ango da amarya basu san wainar da,'ake toyawa ba,Shi saleem bai yarda ya sanar da kowa ba,sai inspector sale,domin shine kadai yasan Shirinsa,ammh shikanshi baisan me yake Shirin aikatawa ba,kuma Tun bayan tafiyarsa baiji yanama sha"awar zuwa gida ba. Shiko Alhaji Abdulmalik,Tuni ya kira chan Malumfashi ya sanar dasu,hakika sunji mamaki tare da al'ajabin jin wannan sangartattaciyar yarinyar zata yi aure? Abun tambaya wani dan asaran ne zai kwasan ma kanshi,haka kowa ya rayawa aranshi,Fatan alheri sukayi da murna,shima anashi barayin Shiri yake na mussaman Domin ana Saura sati biyu biki ya buga kayatattun katina,nashi dana Abbi wanda Direba guda ya tasa yakaima Abbi Abuja,akallon Farko kanama katin zaka Fahimci Abun na manya ne,mai fara fasa Abun Aduniya ba,saboda kada lbri yakai kunnann Malika komai ya tawarwatse. Ana Saura sati daya bikin, kayatattacen ginin da Alhaji Abdulmalik ya sanya ayimai a anguwan GRA katsina ya kammallah wani gida ne upstair mai kyau da tsari bayan yaji makeken haraban mai dauke Da Fulawowi masu dadin kallo da ban sha"awa,wanda akallah zasu ji motoci fin ashirin basu san an ijiye komai ba,Tsarin gidan ko akasar Turai albarka,duk Abunda maleka ke so an ginamatashi acikin gidan,kama daga wajen wasanni,da kuma wajen wanka Swimming Fool,domin kusanta akwai shiga ruwa kamar kwado,Sai Tsarin kayan gida wanda kamfanin MAHARBA tazo ta baje kolinta acikin wannan gida kafin lokaci sun kawata gidan da kayansu na alfarma kalan Red and black duka kayan gidan komai da komai kalansa kenan,domin best colour ne na Malika,mai gayyah mai aiki,dakinta kuwa fadar yadda aka tsarashi bata baki ne,hatta da wasu ubansu sabbin kayanta wandanda take sakawa an Jeramatasu cikin wani makeken wardrope,mai kunshe da gilasai Abun sai wanda yagani. Daki guda aka ware aka jeramata akwatunanta guda 40 wanda Mahaifinta ya dagi kirji ya bada kudi Hajiya binta taje Dubai tahado mata komai da komai na bukarar rayuwa,sai dai kash gabadaya kayan daga Atamfofi da lesuka sai material da kuma dogayen Riguna,babu Zabin Malika ko daya aciki,saboda ana Tunanin zata shiga kwaryan manya,Sauran akwatunan cike suke da kaya shake kama daga takalma,Jakukkuna,Kayan make up,sleeping dress,agoguna da Yan kunnaye Banda Zinare da Azurfa babu Abubda ke ciki,Abun fa sai wanda ya gani,daki ne guda ne aka ware musu suma kalansu Red and black ne,an jerasu gwanin ban sha"awa. Shikanshi dakin Uban gayyar Acp Saleem kumo,kenan wanda ke upstair kusa da jerin dakunan Malika,An tsaramai shi,bayan yaji kayan more rayuwa shima Wardrope guda aka Cikamai da kaya kama daga Shadodi,da yadina babu na banza daga gezner sai yadi mai daukan ido,American Suit kuma na kowani kamfani akwai kama daga Hilfiger,Tommy,Armani,louls,Button Dolce,and Gabbana Bersace,DKNY,dukkansu kalan Bakake da masu Ruwan kasa. Bangaren Turareka da lation kuwa Abun sai wanda yagani kamar za"a budemai shago,balla aje ga bangaren Takalma,gasunan ajere Reras,Kama daga sawu ciki zuwa Rufaffu na Fatar damisa ga jerun agogun nansa na Fata dana karfe na kamfanin Rado,Babu Abunda mutum zai nema ya rasa acikin wannan Dakin,domin duk Abun jin dadin Rayuwa da bukata akwai acikin dakin. Daga haraban gidan kuma ya Faka musu Tafkakan motoci guda biyar Biyu na saleem,Uku na Malika na saleem Daya prado ce,sai dayar kuma matrix ce,sai ta malika Komferesor ce,607  kirar piagion,sai Accord,motocine na gani na Fada,kuma dukkansu sabbi ne, daga kwatano aka shigomai dasu diret kuma nan aka killacesu domin ma mallaka motocin sune zasu Shiga wanna kayatattacen gidan mai kama da Aljannah Duniya. Lbrin Auren bai Fita waje ba,saboda tsoron kada lbri yakaima Malika tun tana chan,kuma jin hakan zai iya sakata taki dawowa gida ta Shiga Duniya yasan halinta sarai,shiyasa bai yarda gidajen Yan jaridu da sauran kafafan yada lbrai sunji batun baba,so yake sai bayan an daura sai afasama Duniya taji komai,Shiyasa Tun sauran kwana biyar da bikin Sukayi waya da Malika wacce daga Amurka,Babban birnin America ta Wuce U.S Taje kaima abokan karatunta ziyara,dagachan kuma england ta wuce wajen Dangin mamarta,Da sukayi waya sai ya sanar da ita tadawo gida nan da kwana biyu saboda akwai Suprise din daya Shiryamata bata kawo komai ba ta sanar dashi Visarta take jira,tana bisa hanyar Dawowa. Ana gobe biki gabadaya duka bangarorin biyun gudajensu ya cika da yan"uwansu,na kusa dana nesa, Gidansu Saleem Tuni yan kumo suka hallarta mata anata shagali,ayayinda katsina kuma yan malumfashi kwansu da kwarkwatansu sun hallata mata da maza,saboda bikin dai zahirin batu za"a yi wadaka da abubuwa domin komai mota ke saukeshi kama daga ababen sha,da kuma snacks da sauran Abinci kuwa tun ana saura kwana uku da biki wani kayatattacen restaurant ke yo odar suna kawowa gidan,Abun sai wanda yagani Joda ma ta iso Tun jiya domin Amminta na sanar da ita tayi alqawarin kallo bazai Wuceta ba,so take ga shin waye mijin na malika,kuma ya malika zata kare matukar taji Abunda mahaifinta ke kulla mata? duk ta anada tambayoyinta ne shiyasa ta tadawo daga mkranta da hanzari domin ganema idonta Abunda ke Faruwa koma nace yana kan Faruwa.. Daga Amaryar har Ango sai daren Daurin Auren suka iso gidajensu,wanda suka tararshi cike da jama"a Saleem bai damu ba domin yana da masaniyar komai,Sadiq ne Maye Tun safe ya iso ya dinga jeramai wayar Shuru haryanzu bai ganshi ba,Shiko yayi niyar daga zamfara su hadu aktsina ne,Ammh ya kama damunshi yasa har Abbi na kiransa,Wani Abun mamaki bai dade da zuwa ba,sai ga ya marwan ya kariso shima,wanda kwata kwata saleem bai so ba,yaso ne kowa yayi zamanshi don zuwan fa harga Allah baida wani amfani,saleema dai tace ayi biki lafiya ammh bazata samu zuwa ba haka ta gayama Saleem shiko yace Gaskiya tayi Dabara don baya gayyatan irinsu dama. Malika ko koda adawo taga dangin Abbanta bata wani damu kanta ba, domin tariga ta raina musu arxiki duk azatonta anzo Maula da cin arzikin da"a ka saba ne,shiyasa bayan sun gaisa da Abbanta ta Shige dakinta bata kara lekowa waje ba don bata son hayaniya sam,kuma ko aranta bata kawo wa ita aka taru ba, domin ko amafarki batata zaton hakan zai Faru da ita ba. *WASHEGARI..*   _RANA BATA KARYA SAI DAI UWAR DIYA TAJI KUNYA..._… Ayau Jumma"a 17/1/2020 Dubban Mutane suka Shaida Daurin Auren *MALIKA ABDULMALIK DANKASUWA* Da angonta *ACP SALEEM KABIR KUMO* Akan sadaki Naira Dubu Dari Hudu da hamsin wanda mahaifinshi ya biya da hannunshi ayayinda wani Baffanshi dake kumo ya karboma Saleem Auren,Itakuma malika Kawun mahaifinta dake Malunfashi ya bada aurenta,wanda ya gudana Ababban masallacin jumma"a dake garin katsina. Daurin Auren daya samu hallartan manyan mutane,kama daga kusoshi agwannati,yan kasuwa manyansu da kananansu,kungiyar direbobi,kungiyar Kwadago ta kasa baki daya,Sevil defence,yan mofal,Yan sanda manyansu da kananansu sun samu katin gayyata zuwa wajen wannan Daurin Aure,sai bayan da"aka Daura aure ne, kana Alhaji Abdulmalik Dankasuwa yabama yan jaridu,da kafar yada lbria sanin Abunda ke Faruwa,ko kafin kace kwabo Tuni lbri ya zaga duniya ta ko"ina Kowani Shafi ka bude na wasop,instergram ne,Fbuk,twitter,duka lbrin zaka gani yana yawo da cewa" *WANI ABUN MAMAKI AYAU MUKA GA TARON DUBBAN JAMA"A WANDA SUKA HADA DA KOWANI MUKAMAI AFALIN JAHAR NAN ANA GUDANAR DA DAURIN AURE BAYAN AN SALLAME SALLAR JUMMA"A ABABBAN MASSALLACIN JUMMA"A DAKE  LAYOUT,SAI BAYAN KAMMALLAH DAURIN AURE NE, MUKA SAMU LBRI DAGA BAKIN SHAHARARREN DANKASUWAN NAN WATO ALHAJI ABDULMALIK DANKASUWA INDA YAKE SANAR DAMU DAURIN AUREN DIYARSA CE WATO MALIKA MALIK,TARE DA ANGONTA ACP SALEEM KUMA,WANDA D"A YAKE GA INSPECTOR GENERAL OF POLICE NA KASA GABADAYA WATO IGP KABIR KUMO,SHIN YAYA MUTANE ZASU DAUKI ABUN,ACE DAURIN AURE YA"YAN MANYA KAMAR IGP KABIR KUMO DA ALHAJI ABDULMALIK DANKASUWA BABU LBRI SAI BAYAN AN DAURA AUREN,SHN BAKU TUNANIN AKWAI LAUJE CIKIN NADI..*? Haka kowacce jarida ke wallafawa asaman Shafinta kama da leadership,Dailytruth etc. Shiko Saleem yana gefe shida Sadiq da ya marwan,wanda dukkansu suke sanye da shadda fara taji kyau harda manyan Riguna da hulansu zannah bukar suna ta hannu da mutane,shiko ango tunda aka daura auren yaji wani Faduwar gaba da kasala duk karkashinsa,da wani zumarshi na ramuwa yaji ya Fitarmai aka,yana jin wani Abu mai kama da nadamar Abunda zai aikata ammh kuma bashi da yarda zaiyi domin bakin alkalami ya rigaya daya bushe,Bai ji faduwar gaba sai daya dinga samun waya ta ko"ina da sakonnin Fatan alheri,da kuma tsiyan yayi aure babu lbrin hatta abokan karatunsa da abokan aikinsa lbri yaje musu,Ya marwan ne yake sanar dashu lbri yazaga duniya don harda hotunanshi da Malika ansamu masu hadashi waje daya an dorashi bisa media akasa an saka *COUPLES OF D YEAR* Shi ahoton yana sanye da kakinsa na yan sanda ne,sanda Sadiq ke numai hoton wanda aka watsashi a Twitter,ya tuna sanda akayi hoton sanda Tsohon Inspector general ke sanya mishi Rank din karin girmanshi ne sanda ya zama ACP abuja akayi hoton,shine aka yanke IGP na lokacin aka hadashi da malika wacce ta ke sanye cikin riga da wando black and white kanta babu dankwal gashinta ta saki jelan ta baya,bayan ta tamke samanshi da band,kunnenta makale da waya,alamar kamar ma tana Tafiya ne,aka yanke hoton aka hadasu, sharrin Na"ura ace tare suka dauki hoton. Kanshi gabadaya ya dau zafi,barin ma sanda yaga Abbi cikin mutane yana ta gaisawa dasu bakinshi har kunni saboda murna da Farinciki,suna wajen har mutane sukafara watsewa,yan jarida ko sunan suna haskawa abubuwan dake Faruwa awajen kai tsaye harshi sun so suji ta bakinsu ya daure Fuska yaki basu dama,Shiko Alhaji Abdulmalik bayan sungama Gaisawa da mutanen da suka gayyata sai gasu sun jero shida Abbi hannunsu sarke dana juna kowannensu yaci Farar shadda harda malum malum,Fuskarsu na bayyanar da Fara"a da kuma Farin cikin dasuke ciki. Haka suka kariso wajensu,wanda dukkansu suka zube suna gaishesu,ammh banda saleem don Fuska yayi yaki bude baki gabadaya domin Gabadaya yanzu kowama haushi yake bashi,Alhaji Abdulmalik ne ya Umarcesu kafin su wuce Abuja zai gabatar musu da wani Abu,nan da nan suka shishshiga mota suda tawagarsu sai Gra. Koda megadi ya bude musu get suka sulala ciki,da mamaki suka firfito suna bin gidan da kallo da alamun dai komai sabo ne kama daga motocin gidan yadda suke lullibe cikin tamfol,Daddy bai yi wata wata ba ya damko hannu Saleem ya zuramai makullaye har guda uku,Tsaye yayi yana kallonsa,shiko kafadansa ya daka yana Fadin"Kowa ya Shaida,Wadandan makullayen naka ne halak malak,daya makullin wannan gidan ne, inda zakuyi rayuwar aure kaida malika,Sauran biyun kuma keys din sabbin motocin dana siya maka ne Gift din Aure amatsayina na Uba gareka..."Gabadaya sai su Sadiq da marwan da sauran mutanen wajen,suka dau kabbara,Shiko saleem suman tsaye yayi aranshi yana Fadin"Kash kayi gaggawa Alhaji,inda kasan Abunda nake shiryama yarka dabaka Bani wadanan kyaututtukan ba..."Ammh Afili ko fadawa jikin Daddy yana matse hawayen karya yana mai godiya,Bayansa yake dafawa yana dariya haka Abbi ma yayi ta godiya,ammh sai da ya nuna dawainiyar tayi yawa gaskiya. Nan suka isa ga motocin aka bude suka gani harda na Malikan,jinjina kai kawai Sadiq yake aransa yana ayyana Dalilin daya sanya Saleem auren Malika saboda kudi ne,Ai basu saki baki sai da suka shiga gidan,daki by daki suka dinga shiga suna ganin Uban Dukiyar da"a Narkama gidan,basu tsinke da al"amarin ba sai da sukaga lefen dayayima Malika boutique Guda ne,aka tara,shikanshi Dakin Saleem din ya basu tsoro,kai Ai nan da nan Sadiq ya yarda da zuciyarsa na dama kwadayi ne da Auren jari yakai saleem ga auran malika Kai,babu shakka ya tsinci dami a akala. Bayan sungama gani suka sanya albarka nan Daddy yake sanar dasu basai Saleem yazo daukan Amarya ba,shida kanshi zai kawo malika har dakinta,kana bai hanashi bayan sungama cin amarcinsu ba ya dauki matarsa zuwa wajen dayake aiki ba,in kuma zai barta nan ne,duk yadda yagani. Saleem yaji dadin haka dama kuma Shirinsa kenan,domin adaren yau yake son dukkan wani Shirinsa ya kammallah zuwa waye garin gobe sai Dai aji bom din ya fashe shikuma kafin lokaci yayi nisa da jaharsa,kilama harda Kasar gabadaya. Daganan gidan hanyar Abuja suka dauka,shikuma Alhaji Abdulmalik da danginsa suka koma gida,ko acikin motar,daga sadiq har marwan Zence suke tare da mamakin uban Dukiyar da aka batar suke,shiko Saleem ko baki bai tsoma musu ba illah danne dannen waya dayake tayi,ammh bayan lokaci kuma ana turomai sako ta waya kuma ya na maida reply batare daya bari wani cikinsu ya ankare dashi, ba Gabadaya zuciyarsa ta kekeshi,ba kamar dazu data nemi ta karaya ba,Abbi na gaba shida tawaganshi da sauran motocin yan uwa da sukazo daga kumo,suma lbrin arzikin da Saleem yatako kawai suke kowa aranshi yanajin dama shine saleem. ____________________ Malika ko tun daren jiya data Shiga dakinta bata Fito ba har gari ya waye,akayi ta hada hadar biki da kuma zuwa daurin aure batasan wainar da,"ake toyowa ba,tana kwance tana barcin gajiya sallar asuba ma,sai wajen 10 tayi bayan tatashi daga barcinta na asara,wanka kawai tayi,dama already Breafast dinta su Dose sun gama jera mata komai,Falo ta Fito daga ita sai wata yaloluwar riga Red colour,wacce da Kadan ta Wuce gwiwanta ,Wayace ahannunta wanda Tun jiya bata bi ta kanta ba,sakonni ta tarar bila adadin tare da kuma da kiran mutane,duk yawancin kiran na abokan kasuwancin Abbanta ne,na kasashen ketare,Abunda ya dauremata kai Shine sakonninsu ,mai dauke da *HAPPY MARRIAGE LIFE MRS SALEEM KABIR KUMO* Abun ya Dauremata kai sosai,har ta zauna bisa daya daga cikin kujerun Falon tana sake cigaba da karanta sakonnin,Abun yabata mamaki ammh sai bata daukeshi wani Abu ba,tana tunanin kila kuskure ne,bata ji jikinta ya saki ba,sai da ta shiga shafinta na Twitter taga hotunanta dana Saleem Rututu ana Dorawa ,Friend dinta suna ta mata Happy marriage life. Jikinta ne ya soma rawa,tafara Zargin wani Banza ne ya nemi bata mata suna aduniya kawai dare daya ya hada hotonta da wani kazami kazamin ma,wai wani Dan sanda,wanda basu iya komai ba sai lalacewa da shaye shaye,wai kuma da sunan mijinta,Kutumar uba ne,lalle kowani Wulakantattace ne, ayau basai gobe ba take son saninshi,taji dalilinshi na bata mata suna,da kuma yimata karya Aduniya Fuuu tatashi ta Fice daga dakin dauke da waya ahannunta Falon Alhaji Abdulmalik dake sama Ta nufa tana kwalamai kira bata damu da Dimbin jama"ar dake falon kasa suna kallonta ba. _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 *Shakira* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Dedicated To my Uwar Room, *ZM CHUBADO* Na sadaukar da wannan bautifull Chappy,gareki Ina so ki sani na *YARDA DAKE* kuma nima nasan Tuni kin gama bani Dukan *YARDAN KI* Son so Fisabillah_ 😘 *9*     "Tana Shiga Falon ta tarar da babu kowa ciki sai wasu baki goggoninta na malumfashi dasuke zaune bisa lumtsuma lumtsumar kujerun Falon suna hira... Kallo Daya tayi musu ,bata kara ba bayan taja musu uban dogon tsaki ba wanda tacema kala ta tsallakesu zuwa bedromm din Daddynta tana kwalamai kira,anan ma wayan Fitowa tayi a hargitse daga Falon tayi Falon kasa bibbiyu take hada Steps saboda yadda Ranta yake amatukar bace,gana Abunda tagani  ga kuma na ganin wayanan zugan yan kauyen da suke zaune musu agida basu Tafi ba. Tana saukowa Falon Tashiga kwalama Hajiya kira muryanta akaushe..."Hajiya...?Hajiya...? Take Fada tana takowa zuwa tsakiyar Falon Fuskarta babu Annuri tana bin mutanen dake zaune da wani wulakatattacen kallo.... Joda ce ta Fito daga dakin Hajiyar tana Fadin"Anty Malika lafiya,...? Kallonta tayi tana wani mele baki a sangarce tace"Bai shafeki ba,juz ina hajiya...? Ta bude baki tayi mgana sai ga Hajiya ta Fito daga wani bangare na gidan tana Fadin"Lafiya malika,ina wanan kiran fa..? Baya taja tana Fadin"Ina Daddy shi nake nema banganshi ba...? Kada kai Hajiya tayi tana karema malikar kallo,da ita da rigar jikinta tace"Bayanan ya tafi daurin aure,ammh nasan yana bisa hanyar dawowa.."yamutsa Fuska Tayi kan tajuya tana kallon mutanen Falon tana fadin"Toh su kuma wadanan me suke jira basu tafi ba,sun zo sun share kafa kamar wadanda aka gayyata wani sha'ani plz nidai su tararra su Tafi ko ni na bar musu gidan... Wata goggon Alhaji Abdulmalik dataji haushin mganarta kai tsaye tace mata",Mu tafi ?muje ina Amarsu ta ango? ai muda tafiya sai mun mika ki gid..."Kai Goggo Baraka don Allah kiyi Shuru..." Hajiya ta katseta da hanzari jikinta na rawa,domin Alhaji Abdulmalik sai da ya gargadeta datayi taka tsan - tsan ko Malika ta Fito kada ta kuskura tabada damar da zata Fahimci Abunda ke Faruwa,shi zai sanar da ita da kanshi,to gashi goggo Baraka Tayi baram barama. Malika dataji mganar bata maida kai ba,Saima mele baki datayi wanda ga duk alamu ya zamanto mata jiki,ta juya gabadaya duwawukanta na wani rawa ,da alama ma ko pant bata saka ba,ammh sai me Abun ne ya shiga mata yawo akunne _Mu tafi muje ina Amarsu ta ango? Ai muda tafiya sai mun mika ki gidan ki.._ Toh me hakan ke Nufi..? Tafada tana kara kallon hotunansu dake yawo A Twitter,da sauran sakonnin Jama"arta. . Hajiya binta harta Fara murna,sai kawai taga Malika ta juyo cikin mamaki tana kallon Goggo baraka kafin tace"Kikace me? sai naji kamar kin ambace ni da Amarsu....? Tafada tana kure ta da ido,Tuni Hajiya binta tayi saurin tarewa da cewa"Tafiyarki Malika bada ke take ba,kawai tana zencenta ne..."Tafada bakinta na hardewa saboda tsoro. Malika bata samu zarafin mgana ba mazan yan Daurin aure suka fara Shigowa,wani kawun Alhaji Abdulmalik ne ya Shigo yana Fadin"Kai yau naga jama"a Bura ube,😂alqur"an harda wandanda banta tsammani ba,duk na gansu,yau gani ga Shugaban yan sanda na kasa gabadaya mukayi hannu dashi duk dalilin Auren Malika,kai babu Abunda zance sai Allah ya basu zaman lafiya kawai mallam".. yafada yana saba babban rigarsa bakinsa har kunni. Turus kowa yayi domin Tundaga shigowarsa har mganarsa Kaf akunnan Malika,wacce Tunda taji zencensa lakkan jikinta ya saki tayimai kuri da ido tana binsa da kallon mamaki,shi da fari baima Lura da ita ba,sai da yaga anyi Shuru ana kallon  barayin datake kana ya kallah,ganinta tsaye yasa ya nufota yana Fadin"Wai ga yar cin Durin uwa"Wani irin banzan dabi"a ce haka kina amarya ammh babu wani kwalliya,sai Fito da wannan banzar Shigar,ke binta kuna me baku Shiryata,ayi amikata gidan mijinta Tunda An Daura aure kuma ai babu jira..."Yafada yana kallon Hajiya binta wacce ta jike da zufa,Shiko ko ajikinsa domin bashi da masaniyar Malika batasan Abunda ke Faruwa ba. Kawai bai ankara ba,sai ji yayi ta chakumo kwalanshi tana Fadin"Wata malikar aka Daura ma Aure...? take Fada idanuwanta sun chanza kala sun yi jawur,dayan hannunta kuma na rike da wayarta,yadda ta ci kwalan babban rigansa sai ka rantse wani sa"an ta ne nan ko ya haifeta ya juya uwa uba kanin kakartace,wacce ta haifi mahaifinta. Gabadaya Falon aka saka salati daidai lokacin da Daddy ya shigo yana Tambayan meke Faruwa ne yaji haniya,ai ba"a bashi amsa ba yaga Malika rike da kwalan kawu Shitu,Zaro ido yayi kafin ya kirata cikin tsawa wanda Tunda aka haifeta baitaba mata makamancin irin wannan Tsawan ba. "Malika....!! Yafada yana Kokarin saba babbar rigarsa wacce ke kokarin zamowa saboda tashin hankali,Jin tsawan da kiran sunanta alokaci daya shiyasa ta zabura ta sakeshi tayi baya Fuskarta tayi ja,ganin Daddyta tsaye yasa ta nufeshi da gudu ta fada jikinsa lokaci daya ta fashe da wani marayan kuka tanayi tana Shessheka. Riketa yayi jikinsa yayi sanyi ganin yadda Malika take kuka,Rumgumeta yayi yana Fadin"Why Babby....? Dagowa tayi kafin tace"Daddy plz tell me d truth,da gaske an Daura min aure yau...? plz don"t say yes Daddy nasan cewa kai Uba ne mai Adalci kuma bazaka taba yimin Abunda bani so ba"? Tafada tana kuka Kallonta yayi kai tsaye yarasa Abunda zaije mata dakyar yace"Injiwa...? waya sanar dake wannan lbrin ba gaskiya bane..."Yafada yana riko hannunta,Fizgewa tayi tana Fadin",Gasu  nan su suka Fada,Daddy kalli wayata kalli Abunda nagani,yana yawo mai zaka kira da hakan,kuma ma infact ma mai wannan taron jama"ar yake Nufi,nafara hango Kamshin gaskiya awannan zence,juz look Daddy ka kalli wannan Hoton ka sanar dani karya ne ba gaskiya bane..."Tafada tana haskomai hotonta dana Saleem da"aka hadashi waje daya. Karba yayi yana kallo,gabadaya kansa ya kulle baida mafita illah sanar da ita gaskiya Dagowa yayi yana Fadin",Comon baby taho muje ciki muyi mgana kinji...? Kallonsa tayi kafin ta ja baya tana Fadi cikin tsawa"Wlh babu inda zani sai ka sanar dani gaskiyan wannan mganar...."Tafada tana huci,Kallonta yayi kai tsaye bakinsa na Rawa yace"E...Eh...Gas...Kiyane,buh ammh bby ki tsaya ki....." "Ya isa....."Tafada cikin dakamai Tsawa kamar wani tsaranta,Idanuwanta sun juye Shuru yayi yana kallonta,Wasu zafafan hawaye suka biyota,kawai sai ta nufeshi,tafara dukansa a kirji tana Fadin"Ka zalunci ne,Ka cuceni bazan taba yafemaka ba,i hate u...I hate Daddy...."Take Fada tana dukansa da alamar ta Fita da hayyacinta,kunya ne da nadama suka lullubeshi na Abunda malika takeyi riketa yake yana kiran Sunanta,ammh bata ko jinsa,illah dagewa datayi tana jifansa da duk kalmar datazo bakinta,harda cemin Azzulumi Ranshi yayi mugun baci baisan sadda ya daga hannu ya kwasheta da maruka har biyu ba, Dama da hauni,wanda sai da ta kife saboda zafin marin nan da nan bakinta ya fashe hancinta yafara habo,yana xubar da jini. Tsaye yayi gabanta yana huci yake Fadin"Ba tun yau Nafara Nadamar sangartaki danayi ba Malika,Ammah yau na kara jadadda Nadama na,kuma na yarda Allah ne yafara nuna mim Isharata Aduniya,ina matsayin Mahaifinki,ammh kirika jifana da munanan kalamai,don kawai na aiwarta da Umarnin Allah,toh bari kiji daga yau na daina Saka rmiki kina Abunda kika ga dama,Tunda ke bakisan mutumci ba,kuma Auren anriga an Daura wlh ko zaki mutu yau nida kaina zan mika ki gidan mijinki,Allah barshi daga chan ki rataye kanki mutu karewar iskanci,Binta kamata ku Shiga da ita,ku shiryata a gaggauce nan da wani lokaci xan mikata gidan mijinta..." yana gama Fadin haka ya wuce sama Fuu kamar zai tashi sama.saboda Fushi itako malika kasake tayi hannunta dafe da bakinta dake jini,Abunka da farar mace,nan da Fuskarta tayi jajir,ga shaidun yatsun nan sun bayyana,saboda bakin ciki da takaichi kukama ya kasa zuwa mata,kwanciya kawai tayi awajen hawaye suna kwararomata,bata ta zaton yau ita Malika malik,haka zai iya Faruwa da ita ba. Tunda tataso wajen Daddynta banda soyayya da zallar kauna babu Abunda yake gwadamata,bai taba saka hannu ya dake taba,kai ko Fada bai taba yimata,koda kuwa tayi ba dai dai ba,tsakaninta dashi sai lallashi da soyayyah,ammh yau na rana tsaka saboda Auren,Auren ma arasa waza"a hada ta dashi sai wani kazami kuchakin Dan sanda,kakin datafi tsana aduniya,tunda take gudanar da rayuwarta bata ta kawowa zata iya aure ta zauna karkashin wani abu,sai dai ko in ita taga kayimata,ta yarda ta aureka,randa ta gaji dakai ta sakeka,dama shirinta kenan koda Daddynta ya mtsamata tayi aure Wani Siririn kuka take saki tana daga kwance,suko tsaye sukai suna kallonta,suna Allah wadai da ita,Hajiya binta ne ta karisa gareta tana dagota take Fadi",Tashi tashi Malika kada ki zama wadanda Allah zaiyi Fushi dasu,ki bi umarnin mahaifinki don yana da hakki akanki,Ki biyashi shekarun daya kwashe yana gina rayuwarki da gata,baki taba neman Abu kin rasa ba,kullum Cikin Faranta miki yake baya son ganin bacin ranki,ke ko daidai da Rana daya baki taba Sashi Farinciki ba meyasa yau bazaki Sashi Farinciki ba,koda sau dayane arayuwarshi ya Tuna yau Malika tayi min Abunda nakeso batare da gaddama ba,haba Malika,don Allah bar kukan nan ki tashi,domin yanzu darajanki ta karu,igiya uku ke reto akanki,wanda bakowacce mace ke samun irin damarki ba..."Tafada tana rikota,haka ta data ita jikinta ya saki banda zubar kwallah bata komai,ga duk alamun mganganun Hajiya binta sun Shigeta,neman Faduwa suke gabadayansu saboda yadda Malika ta sakarmata Nauyinta,da Saurin wata kanwarta dake Malumfashi ta kariso zata rikota tayi saurin Matsawa alamar bata so. Ganin haka yasa Hajiya binta ta yafito Joda da hannu suka riketa kowanne ya sagala hannunta daya bisa kafadansu,suka fara taku da ita zuwa sama,har dakinta suka kaita,Hajiya binta da kanta ta Shiga tiolet din ta hadamata Ruwan wanka,ita kuma Joda tana zaune kusa da ita tana Faman Sharemata hawaye kamar wata karamar yarinya,ammh ranta fal dariya,da sukace tashiga wanka banza dasu da tayi,sai ma saka baki datayi ta kira su merry da Dose sai gashi sun Fito da hanzari da hannu tayi musu mgana,Sai gashi sun dauketa cak sun Shiga da ita bedroom dinta. Suna mata wanka tana kwance cikin bath din Idanunta arufe tana kuka ammh na zuciya,domin hawaye ne ke ta zubomata kamar an bude famfo,sukansu Dose sunji ba dadi,lalle Duk Abunda ya sanya Madam kuka bamai sauki bane,matar data ke jaruma isasahiya mai ji da kanta yau ita ke kuka da idonta. Haka dai suka gama mata wankan suka Fito,da ita koda su shafeta da mayuka,tuni joda ta iso dakin dauke da wani Ubansu leshi mai kyau da yarari,kalan marun,and red,sai takalmin shi da jakarsa da wani katon mayafi red,ammh yana da santsi Kuma sharashara,yake yana da wasu duwatsu kanana masu kayyali ajiki,sai dan kunnen zinare guda daya Wanda mahaifinta yayimata domin zuwa gidan Miji dashi. Mikamusu kayan tayi tana umartansu dasu sanya mata su,sake baki sukayi suna bin kayan da kallo,suna mamaki don dai su a iya tsawon zamansu da Madam bata taba sanya wani kaya ba,bayan Suit,ko kuma wando da riga ko Sikat da riga,ganin yadda suke mamaki yasa tayi musu mirmishi tace"Ur Madam she now a bride today...."Tafada kai tsaye tana kallon Malika wacce ke zaune kan Stool kamar mutum mutum banda kwararan hawaye babu Abunda takeyi,kuma bata damu data saka hannu ta share,ba in ka kalleta sai kazata kamar wata wacce tayi loosing din memary dinta, Zaro ido sukayi cike da murna suka ce"Wow...Congratulation Madame...",Suke Fada bakinsu har kunne,ammh kuma jikinsu yayi sanyi ,Ganin yanayin madam din,da alamun dai bata marada da wannan Auren,ahaka suka sanya mata kaya,Abun mamaki sai gashi tayi kyau cikin kayanmu na hausa Fulani Fiye da na Turawan data ke sanyawa,Joda ita tayimata Dan Simple make up,wanda anayi tana Batashi da hawaye,ahaka aka gama,Ko motsi batayi ba kamar wata waccce lakanta ta cire bata wani karkashi. Suna gamawa sai ga Hajiya binta tana Fadin suma su merry su Shirya kayansu dasu Alhaji yace za"ta tafi,kuma su daukan ma malika duk Abunta mai amfani kama daga abubuwanta na Sirri,ammh banda kayanta jikinsu na rawa suka koma ciki suna hada kayansu,Itako tana Zaune kamar an Dasata,sai ga Alhaji Abdulmalik ya shigo har cikin bedroom dinta ganinta haka bakaramin sosaimai rai yayi ba,karisawa yayi gabanta ya durkusa yana riko hannunta yace *MALIKA..*... Yakira sunanta cikin taushin murya,dagowa tayi tana kallonsa,ammh kuma hawayenta basu tsaya ba,Mikar da ita yayi tsaye yana kallon kwayan idonta yace"Ki yarda dani mahaifinki ne? kuma kin yarda ni bazan taba yin Abunda zai Cutar dake ba...? Zuru tayimai takasa mgana illah Kallonshi datakeyi tana zubar hawaye,Hannunshi ya kara mikamata yana Fadin"In har kin yarda da Soyayyar dani ke miki malika,ki saka hannuki cikin nawa kizo muje na mika ki gidan mijinki....",Yafada yana mikamata duka hannuwanshi... Wajen yayi tsit,ana jiran ganin Malika zata mika ko a"a,sai kawai tabama kowa mamaki,jikinta asanyaye ta mika hannunta cikin na mahaifinta,lokaci daya tana sanya hannunta danashi ta share kwallanta,kafin ta dago Fuskar babu fara'a ko kadan ballatana Annuri,Damke hannuwansa tayi kafin ta Furta murya shake"I Truth u Daddylove....and am very srry For wht i did...",Tafada kai tsaye tana kara nuna dakewarta,jin dadin kalamantane yasa ya Rumgumota yana sakamata albarka,tuni Hajiya binta ta mikamai mayafinta ya saka mata bisa kai,shi da kanshi ya durkusa ya zuramata takalminta mai Dubu ya riko hannuwanta suka Fito daga bedroom din Joda da Hajiya na biye dasu abaya rike da jakar Malika,sai Su Dose da kowacce kowacce rike da jakarsu su murna ta ciikasu zasu koma new House. Ahaka suka fito har zuwa falon kasa,Gabadayan matan dake wajen suka mike suna sakin guda,waje fa ya rude,haka suketa reramata wakan... _Ke kikace kina so,da baki ce kina so ba da bamu baki shi ba.._ Ayyiriri guda ga Amarya zamu kaita Gidan miji zata kwana,zamu je musa kida muyita Tsalle..._ Haka suketa rerawa suna rawa da guda,itako Maleka tana Rumgume da Daddy tana jin kamar ta farka ace mata mafarki take ba gaskiya bane. Haka aka Fice da ita,motar Daddy vibe 2k19 ya saka Malika agidan gaba,shikuma ya shiga mazaunin Direba domin shi zai kaita da kanshi,Sauran jama"a kuma suka shiga sauran motoci domin suje suba idonsu Abinci,lokacin wajen shida ne na yammah ana gabda kiran sallar mangariba. Motar Daddyce tafaryin gaba,sai na Hajiya binta wanda Joda ke ciki da wasu yan"uwa,dai sauran ayarin motocin wadanda sukayi combain,tare da excorts din malika da motocinta,duka domin Alhaji Abdulmalik yace da komin ta zata tafi,cuz bayaso Malika ta chanza,yarda take rayuwarta na baya haka yake so Ta cigaba.    _________________ Suko su Saleem suma koda suka koma gida ya dinke da jama"a anata hidima nan fa lbri ya tashi na irin Dukiyar da'aka narkama Saleem da kuma kyauttukan da Alhaji Abdulmalik ya bamashi saleem,din nan fa wasu sukayita mganganu,donsu harga Allah daga Saleem din har iyayan nashi suna musu kallon kwadayi ne ya kaisu. Shiko Saleem Dakinsa ya Shige ya kulle kansa,saboda cigaba da Shirinsa,baifi minti talatin da Shiga sai gashi ya Fito,da makullanyen gidan,da Daddy ya bashi dana motar da"aka bashi,da kuma anihin key din motarsa,wacce yake hawa,agaugauce ya samu Abbi ya sanar dashi cewa yanzun nan ya samu waya daga chan headquatersu na zamfara ana nemanshi da gaggawa so yanzu zai tafi ne,Abun yabama Abbi mamaki wani irin neman gaggawa ne haka,bai musa mai ba yamai Fatan alheri,ammh sun rabu akan in komai lafiya zuwa gobe zai tafi katsina chan wajen Amaryan tashi,haka ya shiga wajen Ummi yamata sallama,ana ta mai tsiyan ango guda bazai tsaya agama shagali ba,Shidai yake kawai yake baya mgana. Sanda Sadiq yaji tafiyan Saleem zamfara yaso ya bashi yaki bashi dama,dole ya kyaleshi ya Shiga mota ya kama hanya,ya bar garin Abuja yakama hanyar zamfara,bayan yakira wata nomba yana Fadin"Inspector Saleh,gani hanyata ta zuwa zamfara juz tell  me,karfe nawa flight dina zai tashi...?Banji me aka ce mai naji dai yace "Ok mu hadu a Airport din kawai..."Daga haka ya yanke kiran yana wani killer smile bayan ya sakarma motar gudu. Awa biyu ya dauka kafin ya isa zamafara saboda gudun dayayi ko headqutern nasu bai shiga ba gidansa ya Wuce,lokacin anata sallar mangariba amsallatai Shiyasa ya tsaya yayi wanka yayi sallah kafin ya chanza kaya zuwa Uniform dinsa,lokaci daya ya koma aninihin ACP SALEEM KABIR KUMO,madubi yake kallo sanda yake kafa hularsa bisa kai Fuskarnan babu Annuri ko kadan. Cikin Sauri ya dauki wasu takardu,sai pasports dinsa da kuma Atm dinsa ma,'ajiyar kudinsa kenan sai kudi Dollarwanda ya dauka baisan ko nawa bane ya zurasu cikin aljihu ,bai dauki kaya ko daya ba,ya Fito a gaggauce ya kulle gidan,bai bata lokaci ba Shiga cikin headquater nasu nan naga yana ta sallama da ma"aikatan wajen yana barin musu sallahu,Abun da yabani mamaki office dinsa kawai ya Shiga ya dauki wata takarda sai Syestem din shi wanda dukkan Abubuwan aikinsa naciki,ga duk alamu dai kamar Tafiya ce mai muhimmaci Saleem Zaiyi  daga yanayin yadda yake musabaha dasu na bankwana ne,suna fatan Allah yabashi sa"a kuma ya dawo dashi lafiya. Koda yabaro zamfara 7 da wani Abu na dare bai yi wasa ba ya sakarma motarsa gudu yanayi yana duba agogon hannunsa,domin so yake ya isa Katsina kafin goma na dare,domin jirginsa zai tashi ne da karfe 3:30 na daren yau din,jirgin dazai tashi daga kano zuwa kasar CHICAGO dashi aciki,shiyasa yake komai cikin hanzari kuma yana Fatan komai yatafi kan tsari kamar yadda ya tsara.    ************** Alhaji Abdulmalik da kanshi ya Shiga Da Malika har kayatattacen dakinta wanda ya Shiryamata ya kuma mata masauki bisa gadonta,Fuskarta na rufe,ammh kuma tana kallon komai saboda mayafin nada sharashara,kanta kawai ya dafa ya shiga sakamata albarka kafin yayi musu addu"an zaman lafiya hawaye ne yaji suna Shirin tahomai shiyasa yayi saurin Ficewa. Kowa son barka yake da gidan suna jinjina dukiyar da"aka kashe babu wanda aka bari ya dade duka Daddy ya tararra su su koma gidanshii,Hatta hajiya binta bata dade ba tatafi Joda ne ma sai daga baya tatafi,aka bar malika daga ita sai merry da Dose sai su peter dake Haraban gidan suna mazurai. Shiko Alhaji Abdulmalik bayan ya dawo gida ya kira Abbi yana sanar dashi amarya tana dakinta,nan Yake sanar dashi kiran gaggawan da Saleem ya samu da Wajen aikinsa,bai nuna damuwarsa ba,saima fatan alheri dayayi mai yace zai kirasa yanzu,bayan sun gama waya yayi ta kiran wayar Saleem bata shiga,sai yayi Tunanin kila network ne,bai san ko Tuni Saleem ya saka nombarshi cikin black list din wayarsa,domin game din ya kusa karewa. Itako Malika tana jin Diran Fitan motocin gidansu tayi zumbur ta mike tana karema dakin kallo,kayan jikintane suka dameta tafara kokarin cirewa bayan tayi jifa da dankwalinta Merry da Dose take kwalama kira,wadanda ke Falo,da gudu suka Rumtumo suna rawan jiki,Jikinta ta nuna musu tana Fadin"Oy up dis Cloths now.."Tafada cikin Tsawa,jikinsu na rawa suka Nufeta suna kiciyar ciremata less din dake jikinta,tsab suka tubeta suka barta daga ita sai pant,da bra wardrope suka bude suka daukomata wata doguwar riga ta roba,wacce bata da hannu suka zuramata,nan da nan ta lafe mata ajiki,ajiyar zuciya ya ta sauke tana baza gashin kanta da hannu tayi musu alama dasu Fice su bata waje,da hanzari suka Fice jikinsu na rawa da sabon Halin Madam dinsu,Fuskarta kwata kwata babu rahama,duk da ada Bata da mutumci,ammh na yau yafi na kullum.    ****************** Karfe 9:40 Na dare Saleem ya zuba hon abakin get din gidan da"aka zana amtsayin mallakinsa,Megadi yana lekawa yaga Shine da hanzari ya budemai get din ya sulala ciki,Koda ya isa parking space baiyi mamakin ganin motocin Malika ba,Cike da wajen ba,gefe daya kuma Exscort din tane keta shawagi suna zaro ido,dariya yayi cikin ransa yana ayyana Abubuwa da dama. Ya dade cikin motan kafin ya Fito cikin azamarsa na cikakkan Namiji kulle motarsa yayi yana saka duka hannuwansa cikin,aljihun bakin wandon dake jikinsa,taku ya farayi zuwa kofaar da zata sadashi da cikin gidan,ko kallon Su peter bai yi ba,wadanda suka kame gefe suna mazurai domin Tun Fitowarsa daga mota kwarjinsa da haibansa ya dake su,Baya su ja suna ayyana kila wannan ne mijin madam ne,balle yadda suka ga ya hade rai kamar an aikomai da sakon mutuwa. Cikin takama da isa ya sa kanshi Babban Falon gidan yana bin ko"ina da kallo,gabadaya Falon ya cika da kamshin Turaransa na MAN, merry da Dose dake zaune sukayi hanzarin mikewa suna kallonsa,ammh shi ko inda suke bai kallah ba,kuma bai tankasu ba,Steps yafara hawa Still duka hannuwansa na jikin aljihun wandonsa,Har zuwa Dakin daya Haddace cewa Shine na Malika. Tura kofar yayi batare da yayi sallama ba,har ya Rufeta batayi motsin da zan agane wani ya Shigo ba, dan makullin dake jikin kofan yayi amfani dashi wajen Kulle kofar dashi,gefe daya kuma yana Saka key din cikin aljihub wandonsa, yana juyowa Da Malika yafara cin karo wacce ke kwance bisa gado,Ta na kallon kofa ta baza gashin kanta,Har ya Rufemata ido daya bayan idanuwan nata na Rufe kamar mai barci,ga santala santalan Fararen kafafun ta nan awaje saboda yanayin yadda ta kwanta babu inda ya boye na jikinta. Kuramata ido yayi yana jin Wani daci tare da bakinciki na zuwamai,nan da nan Abunda ya faru Shekaru biyar ya dawomai kamar yanzu komai ke Faruwa,cikin takun natsuwa ya isa gabanta yadauki kafarsa daya mai dauke da bakin Takalminsa Sawu ciki ya aza bisa gadon,yana girgizashi da kafarsa daya. Kamar amafarki taji motsi bata bude ido ba tace"Who..? azaton ta su merry ne,ammh sai taji Shuru ranta ne ya baci ya sanya ta bude lumsassun idanuwanta tana bin bakin takalmin dake ijiye gabanta da kallo,kafin ta daga idonta zuwa bakin wandon jikinsa har zuwa rigar Uniform dinsa har zuwa saman kansa,Yadda suka hada 4 eyes cikin wani yanayi na tsana da tashin hankali Saleem ke kallonta yayinda ita kuma Abun yazomata abazata,ammh sai ta dake tana daga kwance tace"Who are u? waya baka damar shigomin gida...? Baiyi mgana ba illah Saukar da kafarshi dayayi kasa yana kara maida hannunuwansa a aljihu zagaye gadon yafarayi yana Binta da kallo,itama tana kallonshi ammh kuma tana jin jikinta na rawa saboda yanayin yadda yake kallonta,Uwa uba kuma wai yau itace tsaye da mai sanye da Uniform din yan Sanda adaki daya? kai ina imforsble,tafada aranta kafin ta mike ta sauko daga kan gadon da hanzarinta sai gata agabanshi. Baya yaja kamar yana jin tsoronta kafin yace"No ba yanzu ba Hajiya Malika juz wait nayi miki wani bayani mana...',Karo na farko daya yimata mgana Zuru tayimai tana kallonshi daga sama har kasa,Zagaye bayanta yayi kafin ya takaro kafarshi da gado,shikuma yasata a tsakiyarsa kafin tayi wani yunkuri ya daga hannu ya zuba mata wani lafiyayye mari mai zafi da gigitarwa wanda sai da tayi luuu zata kife bisa gado yasa hannu ya Fizgota yana huci yace"Kai ne ko? kai kabasu Umarnin su tsaremin motoci ko? Toh daga yau bazaka kara saka atare motocin wani ba,balle motocin Malika malik..."Yafada yana fitar da hucin mganar bisa Fuskarta, Itako Suman tsaye tayi,ayayinda jini ke biyo hancinta da bakinta saboda yadda marin ya gigitata,kalamanshi take son Tunawa,ammh kafin ta samu damar Sakasu Acikin kwakwalrta ya sake kifamata wani marin kamar Allah ya aikoshi wannan karon bai hanata Faduwa bisa gadon ba,ya barta ta Fada,rajab tana Dafe duka kumcinta saboda Taga gilmawan wasu taurari,bai barta tayi motsi ba ya sanya Kafarsa daya ya take mata dan yatsarta daya ya murje,sosai wanda sai da ta saka ihun azaba da kuka,Hannu  ya sa acikin aljihu ya kwaso kudi dollars ya watsamata afuska yana Fadi cikin Tsawa...   _MALIKA MALIK...Sai na Rama..."!_ Kin Tuna don Ubaki ko sai nakara Tuna sar dake da duka? "kin Tunda kakin da kika cima zarafi,..?kin Tuna kakin da kikace basu iya komai ba sai shaye shaye da yi mata Fyade,...?Kin Tuna sanda kika kirasu da Rubbish,..? "kin Tunsa sanda kikace basu amsa komai ahannun mutane  sai na goro dana sigari,...?kin Tunda sanda kikace Basu da wani amfani akasarki,...? kin Tuna...? kin Tuna...? Kin Tuna Hanyar Dutsenma zuwa katsina,Kin Tuna wani Saurayi da kika shararama mari,kuma kika sanar dashi haka..? Kin Tuna ko baki Tuna ba yanzu na kara Tunasar dake....? Yafada yana kara murjemata yatsu,bayan ya zubamata manyan idanuwansa wadanda suka suka koma jawur saboda Bakinciki. Malika data ga Lahira kusa tana ihun azaba ta Furta"Na.Na......Na TU....Tu..Nah....,"Tafada wani tsoro Na Shiganta lokaci daya. _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 Shakira. *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Littafin *MALIKA MALIK* Na kudi ne ki biya akan Naira 200kachal👌ki turo ta account Nomba kamar haka 0552179550 *JAMILA UMAR GTB* bayan kin dauki hoton Sreenshoot din Transaction din,sai ki turomin ta wannan Nombar 09069067488,Ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488 shima kai tsaye bayan an dauki hoton katin sai aturo*_ *I think zan baku 12 free pages ne,so my real Fans,ku hanzarta yin Rigister kafin Arufe bodar banda ku*😘   *10*     ""Cikin gadara da isa yace.."Good,Nasha kin manta ne na kara Tunatar dake...,? Yafada yana kallonta ido cikin ido,kafarsa ya dauke akan kafarta,wacce ya take,sai ya dorata bisa gadon,bayan ya saka takalminsa ya take mata hannu,Kara ta saki tana kokarin dauke hannunta,ammh ina ya take da karfi,saboda Mugunta sai ma ya dinja juya Kafar nashi,takalminshi na barazanar cire mata Fata hawaye take tana yarfe hannu,ammh ko digon tsausayinta baiji ba,illah cemata dayayi   "U better Wipe ur tears yarinya,don kuka yanzu kifara,Bama ki fara shi ba,wlh don Alqawarin dana dauka sama da shekaru biyar,ina jiran ranar da zan Rama Abun da kikamin..."Yafada kafin ya dan dakata yacigaba da cewa"While,bani son batama kaina Suna ne,da kuma sunan Family na,ammh da Tuni na saka an dauko min ke,na yaga miki rigar dan Sauran mutumci data rage miki,domin baki da ita,ammh sai ki kaci darajan ni nasan darajan kaina,Na kuma san yadda Darajan mutumcina dana iyayena yake,dat why na nemi aurenki ba don ina sonki ba,sai don na Nuna miki aikin da kira yan Sanda da suna yi...." Yafada yana kallon gefe kafin ya sauke kafarsa yafara taku yana fadin"kin ci sa"a banzo miki abuge ba ko?..Yafada yana kallonta kafin ya tsaya agabanta yana Fadin"Duk da haka Nayi miki da tsaraban dayan Hali kalli kigani.."Yafada daidai yana warware belt din wandonshi yana kuma cigaba da fadin"Yanzu zan miki fyaden da kikace,kuma da kakin yan sanda a jikina,,kinga ko gobe zaki iya bada lbrin Dan sanda Baida aiki sai yima mata fyade,Tunda yafaru akanki ko...?... Yafada yana kallonta,gefe daya kuma yana cigaba da Zare belt din dake kugunsa,Malika dake kwance azaban hannunta,da kuma marin datasha bai saketa ba,taji wani tashin hankali baya tafara ja,tana kuka,duk Fuskarta tayi ja,batama iya matswan sosai saboda yadda ko"ina na jikinta ke rawa,Kallonta yayi bayan ya gama cire belt din ya dagashi yana kallonta kai tsaye ya kece dadariya yana Fadin"No.No.not now,plz karki tsorata Tun yanzu,ai bamu fara wasan ba,balle mu karkareshi.." Yafada yana cigaba Da dariya karshen gado ta makure tana rawan jiki da baki take Fadin"Plz am srry,am very srry For my mistake,don Allah kada kamin Fyade,i prmise u ko nawa kake bukata zan baka,Nidai juz kayi hakuri...",Take Fada Tana hada hannu,bai saurareta ba sai ma kara sakamata dariya dayayi yana nunata yace"Ayyah Srrry am very srry ko? yafada yana kwaikwayon Muryanta kafin kuma ya koma ya hade rai yana Fadin"Ki Ada kalamanki Madam Malika,yau Babu Abunda zai hanani ban cika Ramuwana akanki ba,so ur better close ur mouth tunkan na Fusata nayi miki dukan mutuwa kan nayi raping dinki..." Jin haka yasa tayi Shuru tana zubar hawaye,bude baki tayi tana kwararon ihun akawo mata dauki,da hanzari ya Zare takalmansa,ya dira bisa gado,ya kara dauketa da wani bahagon mari sai da ta kife bisa gadon,ta dauke Wuta na wasu mintina,gashnta ya damko ya dago kanta yana kallonta Kafin yace"Yau baki da ma cetonki sai Allah....Malik malik sai na rama..."Yafada yana watsar da ita gefe,kan tayi wani yunkuri ya bita ya danne yana Fadin"Nayi alqawarin yadda kika sauyamin rayuwa na rayu cikin Buri da zumar Ramuwa gareki,wlh nima nayi alqawarin adaren nan zan lalata miki dukkan Rayuwarki,daga yanzu an shafe babinki babu wanda zaki kara takawa da sunan tozarci,zan yaga miki mutumci ta hanyar da har Abada bazaki manta dani ba..."Yafada kafin ya damki gashinta kanta ya dago ta yakara makata jikin gado,kamar yasamu yar tsana,Malika naso tayi ihu ammh takasa,bai nemi taba mata ko"ina ba,illah daga rigarta dayayi sama ya rufemata fuska dashi bayan ya sanya hannunshi daya ya rike kanta sosai ta gaza kwacewa,da hannu daya ya ja pant dinta ya yage,dama gashi Wani raga raga,nan da gabanta ya bayyana bai tsaya kallo ba ya Runtse ido lokacin daya saka hannunshi ya zame wandon jikinshi kasa hade da boxers dinshi ammh bai curesu gabadaya ba, Tuni  sandar girmanshi ta bayyana waje🙈🙉 Ware mata kafa yayi kafin ya saita Abun,sai da ya Tusa kai,kafin ya danneta gabadaya,da karfin tsiya yake turamata,duk da gabanta yana tsukene,ammh kuma ya garagara shiga,Kuka da zabure zabure malika keyi tana kokarin kwace kanta,ammh ina Rikon da Saleem yayi mata bana wasa bane. Ganin tana batamai lokaci ya sanya ya kara azama ya dake iya karfinsa ya Shiga da karfi,wanda sai da Malika ta saki wata razananniyar kara kamar wacce zata mutu,tare da daukewar Numfashi,gashi ya danneta ya sakamata karfinshi ko yatsanta bata iya  dagawa,shiko sanda ya Shigeta ji yayi wani Abu Ya zirgamai Tundaga kwakwalwar kanshi har zuwa Tafin karfarshi,wani sanyi tare da Ni"ima ke saukanmai,cikin lokaci yaji ya jike da zufa,haba Tuni yasa hannu biyu ya rike kanta kawai yana zungurarta kamar babu gobe,caccakanta yake yana Nishi sama sama,cikin Lokaci kalilan Saleem yaji hankalinshi na barin jikinshi yana lulawa wata Duniya wanda baita zaton akwaita ba, bayan wanda muke ciki yanzu. Tun Malika na iya motsi da jikinta,ga kanta wanda ya rike tamau bayan kuma ya sanya rigarta ya Rufe mata Fuska,bata iya numfashi sosai,ga azaba saboda ba a hankali yake binta ba hakarta yake kamar ba gobe,Tun tana iya Fizgan Numfashinta harta gagara,tana ji tana gani jikinta ya saki takoma yi lakwas,wanda idanuwanta suka fara Rufe kansu,Tun tana ji da gani har komai ya dauke mata Diff. Sai da ya shafe kyakyawan Awa daya cur akanta yana aikin Abu daya,kafin yayi realising,Kamkameta yayi yana sakin mata Naushinshi,lokaci daya zufa tana yankomai,Numfashi yake maidawa daya bayan daya saboda yadda yakejin yanayinshi kamar bashi ba,Yafi minti goma yana jikinta,kamar wanda aka tsikara yayi Firgigit ya mike yana dirowa daga gado,wandonsa ya jawo sama,ko kallon Malika baiyi ba,wacce jini yayi ma faca face,kamar wacce aka sassarata. Agogon Fatan dake daure A hannunshi ta kalla yaga 1 oclock na dare,zaro ido yayi yana bin Malika da kallo,Yana shafa dan sajensa,wanda yafara Tsiro da gemu,yana bin kafafunta inda jini ya gangaro,duk ya bata Farin bedsheet din,Wani Nishadi yake ji ganin da alamun ma bata motsi,hannunsa ya daka,adayan yana Fadin"Wow..Ni bravo Dole na jinjina ma kaina,Dat great dama haka nake so,Na ci ubanki dakyau..." Yafada yana Daga hannunta yaga ya biyoshi sharaf,ya Fadi,wani mirmishi ya saki yana fadin"Good...Ashe ina da lafiya sosai...? Yake Fada yana yar dariya,baya yaja yakallon agogon hannunsa again kafin yayi azama ya fada Tiolet din dake dakin,agurguje yayi wanka ya Fito,kai tsaye ya gyara zaman kayan jikinshi,yana daura belt din wandonsa,sai da yagama ya sanya Takalminsa,kafin ya karisa gareta,. Fuskarta ya bude yaga yadda hawaye suka bushemata bayan bakinta ya kumbura,hancinta ko jini ya zubo duk ya bushe,Fuskarta kuwa shaidan tafinsa ne,sukayi male male,Dariyar jin dadi yayi kafin ya daki kumatunta yana Fadin"Ke tashi,tashi mana ki karbi takardan *SAKIN KI* ai bana afi na barki da Nauyi na ba.."Yafada yana bubbuga kumatunta,ammh ko motsi batayi ba,bai damu ba illah Dube dube da farayi yana neman Abun Rubutu,Side drower din gadon ya bude sai ga tarin takardu,da hanzari ya zari wata farar Paper ya dorashi Fuskarta yana kallonta yana wani mirmishi mai kama da mugunta,Ya fara Rubutu kamar haka..   _*NI SALEEM KABIR KUMO NA SAKI EX-WIFE DINA WATO MALIKA MALIK,SAKI DAYA BISA DALILIN CEWA BANTA SONTA BA,ASALIMA NA AURETA NE DON NAYI ALQAWARIN SAI NA RAMA,TOH SHINE BAYAN NAGAMA RAMAWA,NA BATA TAKARDANTA KADA TA DINGA GANTALI DA AURENA AKANTA,ANA ZAGINA,TUNDA TAGAMA MIN AMFANI GWARA NA SAUWAKE MATA,DAGA KARSHE INA MAI NEMAN AFUWARKA DADDY,DAKAI DA IYAYENA BA LAIFIN KOWA BANE SAI MAHAIFINTA DOMIN SHI YA BATA TARBIYAR YARSHI DA KANSHI,DAGA KARSHE INA MAI SANAR DAKU SAI TAYIMIN IDDA,DOMIN NASAN KO BAN FADA BA ZAKU GA ALAMUN NA DORA MATA NAUYINA,GA KEYS DIN GIDANKA DANA MOTARKA NAN BANA BUKATA DAMA ABUNDA NAKE BUKATA KENAN,KUMA NAGAMA AIWATAR DA GUDURINA SO YANZU D GAME IS OVER NOW*_                                  _Ex huband din yarka Saleem kabir kumo_ Haka ya rattaba kafin ya Kamo hannunta ya sakamata cikin tafinta ya damkematashi na tsawon lokacin kafin ya saki,duk da hannu yayi taushi,ammh takardan ta samu matsugguni,mikewa yayi yana gyara tsayuwarshi kallonta yake kafin koma yakoma ya duka ya saka kanshi saitin zuciyarta,sai yaji yana harbawa ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ciro makullin gidan dana motocin guda biyu ya Zubesu bisa jikinta,ko kara kallonta baiyi ba ya saka kai ya fice ransa fayau yana Fadin *D game is over Now...*.." Yafada yana Ficewa da sauri. Abun da ya bashi mamaki su merry na Zaune basuyi barci ba,suna ganin Fitowarshi suka mike suna zaro ido,wani banzan kallo ya watsa musu kafin ya wucesu da sassarfa har ya kusa Ficewa Daga Falon ya waiwayo yana kallonsu,Suko suna ganin ya juyo suka kamkame juna jikinsu na rawa,saboda yadda idanuwansa da Fuskarsa suka basu tsoro,tsaki yaja yana Fadin"Oya..." Yafada yana nuna musu saman Dakin Malika Baima kai ga mgana ba,suka Rumtuma saman da gudu,domin duk ihun da Malika tayi akunnensu,suma tsoro ne yakamasu suka kasa komai,Yana ganin sun nufi sama ya Fice daga falon da gaggawa,Yana zuwa yayi ma motarsa key bai ga kowa ba,kila su gardawan nata sun gaji ne sun kwanta,ya Shiga motarsa hon ya zubama megadi wanda yazo da hanzari ya wangalemai get ya Fice yana kokarin daurama kanshi Seat belt,daidai lokacin daya duba agogon ahannunshi 1:30pm na dare, kawai sai ya karama motar speend,nan da nan ya Fice Daga garin katsina. Hanyar garin kano ya nufa adaren Ransa Fes sai zuga gudu yake yi Abunshi hankalinshi kwance,cikin  awa daya da rabi sai gashi ya isa cikin babban filin jirgin *MALLAM AMINU INTERNATIONAL AIRPORT* Yana kokarin fakin din motarsa ne,naga wani wanda ke sanye da bakaken kaya ya, kariso wajen motan,da hanzari ya Fito,bayan ya leka baya ya dauko jakarsa ta brief case dinsa ya sagala akafadansa hannu ya bashi sukayi musabaha,kafin ya mikamai pasport dinshi tare da Visarshi yana Fadin"Yallabai saura minti Talatin ne jirgin naku ya tashi,so zaka jira wajen da masinjoji suke jiran tashin jirgi.."... Jinjina kai yayi kafin yace"Tanque So much Inspector,aikin ka na farko ya kammallah,saura na karshe plz kafin safe ka tabbatar ka yada wannan lbrin akafafen yada lbrai,kaji ko.."Amsa mai  yayi da Fadin"Insha Allahu yallabai da zarar jirginku ya tashi zanyi yadda muka tsara,Allah ya kaiku lafiya."Hannu suka kara rikewa kafin Saleem ya damkamai key din motarshi yana Fadin"Sai kajini..."daga haka suka rabu,shi yafada motar Saleem din,shiko saleem ya nufi cikin Aiport din, da sassarfa,daga ganin yadda yake tafiyan zaka san yana cikin niahadi ba kadan ba.   _________________ Dose da Merry,suna bugan kafadan Juna wajen Shiga dakin,Suna shiga suka tsaya agabanta,suna jiran Umarni Tunda sun saba haka take musu,ammh sukaji Shuru,Dose ce ta lura da halin da madam ke ciki afirgice ta nunama Merry jinin data gani ya bata ko"ina. Tsorata sukayi suka nufeta atare,suna Fadin'Madam..Madam..."Shuru ba mgana,hannunta suka daga yakoma ya kwanta baya Dose taja baya tana FAdin",Jesus...." Tafada a firgice kamar zata Shide,Kafin ta kalli Merry bakinta na rawa tana Fadin"She is death.."Girigiza kai merry tayi Hankalinta amatukar tashe ta Rumtuma tafito daga dakin Dose ta mara mata baya,suka fito har haraban gidan suna ihu da kuka,sai gasu peter sun Fito suna mazurai. Suna tambayansu Lafiya,ammh sun kasa mgana sai nuna cikin gida suke suna kiran Sunan Madam,Suma kansu Firgita sukayi Joy keda Nombar Alhaji da hanzari ya latsashi ya kirashi,shiko Daddy yana kwance baisan dalili ba yakasa barci saboda yadda gabanshi yake fadi,sai ga wayar joy,Tunda yaga nombarsa hankalinsa ya tashi da azama yadaga kiran tun kafin yayi mgana joy yace"Alhaji come now,Something bad is happen wit madam oo..."Yake Fada Shima cikin rawan jiki,ko kafin Daddy ya samu zarafin mgana ya yanke wayar. Agaggauce ya sauko daga kan gadon jkinsa babu inda baya rawa,Hajiya binta ya bubbuga yana Fadin"Hajiya.Hajiya..."Da Sauri tatashi tana mutsike ido take Fadin"Lafiya Alhaji...? Jallabiyansa yake zurawa yana Fadin"Ina fa lafiya,yanxu nan masu tsaron malika suka kirani,wai babu lafiya wani Abu mara kyau yafaru da madam.." Da wani hautsinawa Hajiya ta diro daga kan gadon tana kokarin yayiman Mayafinta ta aza bisa rigar barcinta tana Fadin"Innalillah..Toh meya faru ne..? Take Fada ammh kafin ma takara cewa wani Abu,Alhaji ya fice da hanzari,Hajiya binta tabishi da hanzari bayan ta dauki Makullin motar dake kan Side drower saboda Rudewa bai tsaya dauka ba. Ba wanda yasan Fitarsu domin lokacin 4 saura ne na Asuba,hankalinsu tashe suka isa gidan,ko da suka isa sun iskesu duka aharaban gidan,ganin yadda su merry ke kuka ne,yasa daga Daddy har hajiya suka Rumtuma zuwa cikin gidan kamar zasu Ture juna,Daddy shi yafara shiga dakin na Malika halin daya gantane,yasa ya tsaya cak,jikinsa na kyarma,hajiya binta ne takarisa gareta tana karemata kallo daga sama har kasa kafin ta dago hannunta tana Fadin"Malika..Ke malika..."Taji Shuru baya taja ta goge zufan jikinta take Fadin"Allah sa badai kasheta akayi ba... Fadar haka yayi daidai Da Daddy ya zube kan kafafunshi yana kiran Sunan Allah,Hajiya binta ma Salatin dake,sai alokacin idonta yakai kan jinin dake gefen kafafun Malika da hanzari ta jaye rigar jikinta,Salati ta saka tana Fadin"mun Shiga uku Alhaji Wlh Fyde akayi ma Malika...", Jin haka yasa ya mike yana Fadin"Fyade kuma? ya maimata cikin Fitan hayyaci,Gyadamai kai tayi hawaye na zubomata,Hannun Malika ta gani yana matso tayi saurin zama kusa da ita tana dagota tace"Alhaji da Ranta duba kagani hannunta na motsi..."Shiko hankalinshi baya wajenta yanaga makullayan gida dana motar daya damkama Saleem su dazu da rana,mai yakawo su zube kan gadon Malika, Bai gama mamaki ba,ya hangi wata Farar takarda tana kokarin Fadowa daga hannunta lokacin Da hajiya binta ke kokarin dagata tana Fadin"Alhaji tsayuwa ba namu bane,kamata muje asibiti..."... Kamar wani yajashi sai gashi gabanta ya saka hannu ya dauko takardan Jikinsa na rawa ya warware yafara karantawa a bayyane,ko kafin ya gama hawaye sun gama jikamai Jiki,ga wani jiri dake dibanshi sai daya Dafa bango yana kiran sunan Allah,Hajiya binta ta fashe da kuka tana Rumgume da Malika take Fadin"Kagani ko Alhaji,dama wannan Ranar nake jiyemaka Ranar dakai  Da malika zaku fara girban Abunda kuka Shuka,meyafi wannan Cin zarafi,ace aci mutumcinka adaren aurenka,kuma abaka takardan saki adaren...? take Fada tana kuka harda majina,Shiko Alhaji Abdulmalik zaman dirshan yayi yana kuka Wiwi kamar karamin yaro. Itako Malika saukan hawayen hajiya bisa Fuskarta,yasa ta farka daga Suman datayi,idanuwanta take kokarin budewa jinta tana jikin wani,Zabura tafarayi tana wani kame jikinta,kamar wacce wanI shoking ke janta,Da hanzari hajiya ta mike tana Fadin"Alhaji kalli kaga Abunda Malika keyi..? mu dauketa zuwa asibiti..."Ganin bayama cikin Hayyacinsa,yasa tayi waje da gudu ta kira su Dose sukazo suka kama mata Malika,suka dauketa zuwa mota,shiko Alhaji sai da Hajiya tazo ta kamashi ya iya mikewa,Ko driving din bashi yayi ba,Deraban Malika ya tukasu zuwa General hopital. Suna zuwa aka amsheta da gaggawa zuwa emargency,wanda Tunda suka Shiga da ita,har wajen Shida na safe Shuru basu Fito,shiko Alhaji, Abdulmalik kamar wani Mutum Mutun baya mgana sai kuka da sharan kwallah,Tun hajiya na lallashinsa hartazo ta zuramai ido,domin kuka fa yazama dole... Chan gida kuwa anata cigiyarsu ba"a gansu ba gashi duka wayoyinsu sun barsu gida hankali fa yatashi balle da Joda ta ci karo da lbrin asocial media yana yawo cewa *LABARI DA DUMI DUMINSA,AUREN DA"AKA DAURA NA DIYAR SHAHARARRAN DAN KASUWAN NAN DA YARON IGP,TO KUMA AJIYAN MUKA SAMU LBRIN YA DANKARAMATA SAKI,WAI SHIN JAMA"A YA KUKA KALLI WANNAN AL"AMARIN? TABBAS AKWAI ZENCE CIKIN DUHU*Hankalinta tashe take sanar da mutane Abunda ke Faruwa nan fa gida ya rude da hayaniya ga wayoyonsu duk suna gida,ita kanta malikar wayarta na shiga ammh ba"a dauka,cikin wannan Halin wasu mazan suka tashi suka tafi gidan Malika chan sukejin lbrin Abunda ya faru da kuma asibitin da suke,basai kai ga komawa gida bama,suka rankaya sai asibitin koda sukaje har zuwa lokacin likitoci basu ce komai akan Malikar ba kuma tana cikin emargencyn basu Fito da ita ba. Achan gidansu Saleem da Abun suka tashi Domin Tun asubayin Fari Ya marwan da Sadiq suka ci karo da Abunda ke yawo hankalinsu tashe suka sanarma Abbi,nan fa cike da mamaki sukayi ta gwada kiran lambar Saleem,ammh akashe sai suka koma kiran Na Alhaji Abdulmalik ammh shima still tana ringing no answer hankala fa sun Tashi nan da nan Abbi ya sanya aka kira chan headquater nasu Saleem ana tambayansu nan take suka sanar dasu cewa jiya jirginsa yatashi zuwa kasar chicago,domin karo cos din da ma"aikata ta turashi na wata uku. Jin haka yasa gabadaya jikinsu yayi sanyi,domin ga duk alamun akwai kamshin gaskiya,don su basu san da lbrin Tafiyar saleem ko"ina ba,Nan da Abbi yace su marwan su Shirya su tafi katsina suga meke Faruwa,Hajiya babba ko Hannu ta aza bisa kai tana salati tare da kunduma Saleem Allah ya isa,Itako Ummu Zuru tayi tana mamakin ace Dansu da suka haifane ya saki matarsa tun daren Biki,to Abun tambaya bashi yace yana sonta ba ,aka daura mai ba..? bata da me amsa mata wadannan Tambayoyin dole ta hakura,Tuni gidan biki yakoma gidan jimami da takaichi.   ****************** Karfe 10:30am na safe su Abbi suka isa gidansu Malika nan sukejin mugun lbrin cewa Tun daren jiya suna asibiti da ita,Basu tsaya ba,Tunda suka ji sunan Asibitin suka rankaya zuwa chan,Wani Abun tashin hankalin da sukaje suka tarar shine bayan Malika dake kwance cikin halin ciwo,Shima Alhaji Abdulmalik tun bayan bayanin da likita yayi misu na irin illar da Saleem yayima Malika,don yayimata raga raga ne,bai shigeta da sauki ba,domin sai da suka dinketa sosai bisa yadda ya lalata wajen sosai,kuka yakasa zuwarmai saboda Takaichi da Nadama,Illah jin Likitan kawai yake sanda suke Fadin yakamata su Shigar da karar duk wanda ya aikata musu haka. Ya Fito daga office din kenan Yaji joda na fadin Irin yadda mganar Sakin na Malika ya zaga Duniya,babu inda lbrin baije ba,Jiri ne ya kwasheshi ya zube kasa babu Numfashi,Shima haka aka kwashe zuwa ciki domin bashi taimakon gaggawa,Koda su Abbi suka kariso babu wanda yayi musu mgana banda Hajiya Binta wacce ta mika musu takardan da Saleem ya Rubutu,Abbi da hannunsa ya karba ya karanta,yana jin kunyar Duniya duk ta lullubesa,tun takardan na hannun Abbi marwan da Sadiq suka karanta Abunda ke ciki,sunma kasa mgana saboda Shiga Rudani da mamaki ko amafarki babu wanda yayi zaton Saleem zai aikata hakan. Abbi saboda bakincikin kunyar da kuma Yadda Saleem ya bata mishi suna aduniya sai da yayi kwallah,Wani Abun tashin hankali kuma da sanya Raunin zuciya bayanin likitoci kan Fadauwar Alhaji Abdulmalik,wanda sukace zuciyarsa ta harba jininsa yayi bala"in hawa yanzu haka sanadiyar Faduwar dayayi yasamu Shanyewar barin jikinsa na dama. Gabadaya yan"uwansa haka suke kuka suna tsinema Saleem,da irin cin Amanar dayayi musu,itako Hajiya binta Faduwa kasa tayi hannu bisa kai tana karanta Hasbunallahi wani"imal wakil,Lalle bawa bai isa ya Wucema kaddaransa,ammh wannan Abunda ya faru tasan hakkine da kuma alhakin irin Abubuwan da Malika take aikatawa,wanda mahaifinta Shine silan komai... Abbi shima banda salatin Babu Abunda yake Furtawa,sai gashi an gunguro Alhaji Abdulmalik zuwa wani daki na musaaman,yayinda ita Malika itama take wani killataccen daki domin samun hutu,,Abbi ko yana share kwallah ya Fito daga Asibitin su Marwan suka Rufamai baya sun Shiga mota kenan Abbi ya kalli marwan yana Fadin"Ka Turama saleem sako ta E-Mail dinshi ka sanar dashi nace Wlh tallahi matukar bai janye sakin dayayima Malika ba,Toh ni Kabir kumo na cireshi har abada daga cikin ya"yana..."Yafada yana jin kamar ya kurma ihu saboda Nadama. gyada kai Marwan yayi yana Fadin"Toh Abbi..."Daga haka motar tayi Shuru suka Fice daga asibitin suka dauki hanyar Abuja,Shiko Sadiq kara gwada nombar Saleem yake,ammh bata aiki sam,sai kawai ya hakura,ammh shima yayi alqawarin Turamai sakon Abunda ya aikata ta E-mail dinshi.. Kuyi hakuri da Typing errors,ban samu lokacin Editing ba. _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 *Shakira* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*?? _Littafin *MALIKA MALIK* Na kudi ne ki biya akan Naira 200kachal👌ki turo ta account Nomba kamar haka 0552179550 *JAMILA UMAR GTB* bayan kin dauki hoton Sreenshoot din Transaction  din,sai ki turomin ta wannan Nombar 09069067488,Ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488 shima kai tsaye bayan an dauki  hoton katin sai aturo*_ *I Dedicated dis page to u guyzs MALIKA MALIK PAID GROUP,and HAFNAN AND JANAF PAID GROUP,Tanque Dearests,For u true Love and Support,and A big Thanks to u For ur wonderfull and Amarzing commenting, Sakallahu Fil Jannatul Firdausi Ameen*🙏   *11*   "Da wannan bakin lbrin su Abbi suka koma ma su Ummi,wanda suma Abun yadakesu sosai,Abbi kuwa daki ya shige,ya kwanta yayi Shuru cike dadamuwa domin Tundaga wayewar gari zuwa yanzu baisan adadin mutanen da suka kirasa ba,suna tambayansa,game da al"marin ba,Toh mezaice musu banda eh,Domin bashi da ikon boyee Abunda ya Fito Fili,gabadaya kunyar Alhaji Abdulmalik da Duniya gabadaya ta kamashi,yarasa ina zai saka kanshi,saboda yana Tunanin koda zai kwana yana rantsuwan baisan gudurin Saleem akan Malika ba,wlh karyatashi za"ayi,Tunda da kafarshi ya taka yaje nema masa auren nan,ammh wlh ko alama baida sani game da mugun kudirin Saleem. Abunda yafimai Ciwo shine yadda Saleem ya ci mutumci Malika,kuma ya tozartata mafi munin Tozarci kamar wani dabba,wanda baije mkranta ba,ko wanda bai taba sanin Addinin ba,ai duk mai cin zarafin mace dan akuya ne,kuma duk mai Ramuwa kan mace tayimai Abu bai cika jarumi,macen da"aka halliceta da hakarkarinka,kafita daraja ta ko'ina kana gaba ita akowani fanni,kai Shugaba kake gareta,ammh saboda sakarci kakoma bayanta kana wani kunfar baki,Haba ai aiko anyi asara ba kadan ba,Shi ji yake kamar Saleem ba jininsa bane,Tunda har zai iya tozarta mace,wanda Shi Tunda yake baitaba kwatanta ynkuri tozarta mahaifiyarsu ba,balle yace gado yayi ko kuma Abunda yaga anayi ne ya kwaikwaiya,Toh ba daya kanwar Biyu kawai Duniyace tare da Shedan suka kulla Abota dashi yaci zarafinta,daga karshe ni kuma ya batamin suna,ammh bakomai Duniyace ta ishi wanda baizo bama,ballatana wanda ke cikinta,Haka Abbi yayi ta sake sake aransa,Abun yaki barinsa ko kadan. Sai da Ummi tazo tayi ta lallashinsa,tana bashi baki kana ya dan sausauta damuwarshi,yana kada kawai,domin Shi kadai yasan Abunda ke ranshi,na bakinciki da takaichi,haka mutanen kumo suka koma suma da lbri mara dadin ji,Itako Hajiya Babba baki ta rike tana Fadin"Anya ni kabiru shigan Salihu aikin yan sandan ba shaye shaye yaje yafara ba..? Ya marwan ne yace"Ba wani shaye shaye Hajiya,dan iska ne kawai,kuma ba komai yakeso yaga ya cimma ba,sai bata sunan Abbi aduniya,kuma ya aikata hakan shikenan aie..",Yafada yana huci Girgiza kai Hajiya tayi kafin tace"Anya ni ina tamtama kila dai yafara shan Wiwi ne aboye ba"a sani ba,ammh cikakken mutum mai hankali bazai aikata Abunda ya aikataba gaskiya.."Tafada tana jadadda Bayaninta,ba wanda ya sake kulata,domin kowa yasan Saleem ko taba bayashi tsabar Wulakanci ne da tozarci kawai,Shi kanshi marwan Saboda halin da"ake ciki ya sa yakara kwana biyu kafin yakoma,rana daya Suka wuce da Sadiq. Itako Saleem dataji lbrin Abun yayi mata dadi,domin tace Abunda ya saleem yayi Shine daidai,domin ita haka kurum ta tsani Malikar wlh,taji yadda aka koyamata Hankali,tayi kokarin kiran Layin ya saleem,din ammh bata tafiya,sai da sukayi waya da Sadiq ne yake sanar da ita ai Saleem baya kasarma,shi ya sanar da ita Abunda ya faru da Malikar da mahaifinta,wanda ko alama bata tsausaya musu ba,sai ma Allah kara datakeyi acikin zuciyarta,gefe daya kuma tana sakama Saleem Albarka.   ***************** Kwana uku kenan da Faruwar al"amarin Inda Malika ta farka,tunda ta farfado,ta kuma dawo daga hayyacinta ta tuna dukkan Abunda ya faru da ita batayi mgana ba,illah kuka datake tayi,wanda baya da Sauti sai dai kaga hawaye nabin gefen idonta yana gangarowa,komai sai an mata bata iya zama saboda Dinkin da akayi mata akasanta,wadanda dai ada ta raina su ke dawainiya da ita,Hajiya binta da joda,wadanda tsausayin Malikar yakasa barinsu sutuna Abunda tayi musu abaya,Bata iya mgana sai dai kallo da ido,bini bini kuma sai kuka.   Ayayinda Alhaji Abdulmalik kam jiki sai godiyar Allah,domin bakinsa ya karkace baka iyama jin Abunda Yake fadi saboda baknsa babu Dadi,ammh kowa ya Fahimci Malika yake tambaya,wacce kuma anki sanar da ita Halin dayake ciki ne kada takara shiga wani hali. Yan Malumfashi Sun koma,illah Kawu Shitu da"aka bari sai yadan kara kwana biyu,saboda ya taimakama Hajiya binta da jinya,Tunda Masu laluran guda biyu ne,kuma ita kadai bazata iyaba,Don ma Joda na tayata kula da Malika,shiyasa Abun yazo mata da sauki. Sai dai Malika tayi sati kana tafara koyon zama da dubara,kuma aranar ne tayima Hajiya mgana tana tambayan Daddynta,Dafa kafadanta tayi tana Fadin"Ina so ki saurareni dakyau Malika,ki kuma yi hakuri da Abunda zan sanar dake,bisa faruwar Abunda ya Faru dake,shiya yi sanadiyar Faduwar Mahaifinki har Dalilin haka yasa ya kamu da ciwon barin jiki,yanzu haka shima yana kwance acikin asibitin nan.." Zaro ido tayi kafin ta fashe da kuka tana kokarin tashi,ta riketa Tana lallashinta,ammh ko sauraranta batayi kukatake Wurjanjan tana kiran Sunan Daddyta nan Hajiya binta ta kalleta tana Fadin"Kidaina kuka bari likita yazo indai da yuyuwar zuwa ki ganshi sai na kai ki ki ganshi,ammh tabbas Alhaji yaga jarbta asakarma ka y'a adaren Aurenta,kuma bayan angama cin zarafinta...,"Tafada tana jin kunar Abun. Cak Malika ta tsaya da kukan datakeyi kafin ta Dago tana kallon Hajiya Binta tana Fadin"Saki kuma..? Ta ambata tana jin  wani iri acikin jikinta,gyada mata kai tayi kafin tace"Kwarai da gaske,bai barki ba,sai da ya Rubutu miki takardan sakinki Malika,bayan ya dawo ma mahaifinki dukkan kyautan dayayi zuwa gareshi,kuma ya sanar dashi cewa bai aureki don yana Sonki ba,sai don ya rama Abunda kijayimai...."Kuka yakara kwacema Malika,tanayi har takoma Daga kwance tana Tuna kalaman Saleem inda yake Fadin _Zan Lalata miki Rayuwa adare Daya,kamar yadda kika lalatamin nawa a Shekaru biyar da suka Wuce.._ Shi kawai take tunawa tana tsiyayan kwalla,Tana kuma jinjina kai,bata gama Tunani ba,Hajiya binta ta katseta da cewa"Kuma yanxu amganar dani ke miki,baya kasarnan akace Tun ranar daya aikata gudurinsa yasa kafa ya bar kasar gabadaya,Abun takaichi da haushi kamar yadda Aurenku ya game Duniya haka lbrin sakin Aurenki yagama zaga Duniya,saboda rashin adalcima muna Asibtin nan,Yan jarida sun zo har nan,suna kokarin jinta bakinmu akan gaskiyan Abunda ake yawo dashi Aduniya..."Ai sai Malika taji kamar zata Shide,yanzu kamar ita Malika malik,itace wannan Abun ya faru da ita kamar amafarki,yanzu duk jin kanta da yansda maza ke tsoronta,ammh an samu mai Wulakanta rayuwata haka bayan ya tozartani..? take tambayan kanta tana kuka harda rike kai. Kallonta Hajiya binta tayi cikin tsausaya take Fadin"Kuka yazama dole Malika,ammh kuma bazan gaji da Furta muku wannan kalmar ba keda Alhaji,wlh ko kaffara ba zanyi ba,Allah ne,ya turo saleem ne cikin rayuwarku keda Mahaifinki domin ya koya muku Hankali,kuma ya nuna muku Akwai Abunda kudi da takama bazasu taba baka ba,yanzu Duk kudin Abbanki bai isa yadawo miki da budurcinki ba,kuma bai isa ya dawo dake Daga Malika bazawara,zuwa Malika budurwa wacce batataba aure ba,Bai isa ya kankare ikon rabbi ba,Domin bakin Alkami ya rigaya daya bushe,Da ace ke dashi kun dauki Nasihata,da kuma mganata akan ki gyara rayuwarki,da duk haka bata Faru ba,ammh kuka kekesa kasa kuka jina,kuna ganin kamar ina Takura miki ne,gashi yanzu komai ya kwabe Zakuyi Nadama sanda bata da amfani . "Tafada tana Share kwallah. Hannuwanta ta sanya ta toshe kunnata,tana kuka harda jijjiga,kamar wata mahaukaciya,bata son mganar,ji take kamar ace yanzu ta mutu kwata kwata bata Aduniya,da wannan Abun kunyar dake rayuwarta,Ranar dai Wuni tayi kuka kamar wacce ta zauce,sai da akayi mata allurar barci kana aka samu sauki. *BAYAN KWANA BIYU* An samu cigaba sosai abangaren Daddy,wanda har ana iya Fahimtar mganarsa,kuma hakan ya samo asali ne,daga Ganin dayayima Malika taji sauki,haka ta Rumgumeshi tana kuka tana Fadin"Am srry Daddy it my Fuilt..."Take fada,shiko hawaye yake yana Fadin"A"a babby,ba kuskurenki bane nawa ne,da"ace Tun farko na doraki kan Turban da Addininmu ya koyar ban barki kara zube ba, na tabbata da baki hadu da saleem ba,balle har ki cimai zarafi ya biyo yaba yayi ramuwa gareki,na dora laifin duka akaina babby,..."Yake yana tsiyayan hawaye,kawu Shitu ne yasa baki yace in bai bar kuka toh Malika bazata kara zuwa wajensa,ba shine yasa ya daina kuka,ammh ya kafe ta da ido,yana hango tsabar rama da kuma yadda komai na Babby ya chanza,tana zaune Shuru tayi tagumi bini bini kuma ta hau sharan kwallah. Kwananshi hudu da fara Fitar mganarshi Su Abbi suka zo gaishesu Shida Ummi da hajiya babba,Wanda Abbi ya rike hannun Alhaji Abdulmalik gam yana ji kamar yayi kwallah,yake Fadin"Wlh Tallahi,Na rantse maka harga Allah Abdulmakalik da zuciya Daya nazo neman ma Saleem Auren Malika,bani da masaniyar Komai game da Shirinsa,Don Allah kayimin aikin gafara hakika da inada sani kan komai,wlh da ban bada goyin bayan ya aureta ba,ballantana har ya cimata zarafi...",Yafada cike da kunar zuciya. Mirmishin yake Daddy yayi kafin yace",Haba Kabir,har sai ka Rantsemin ?yau kake tare dani,Wlh na sani karka damu kanka babu komai,ni ne silan Faruwan komai,domin na bada dukkan guduMuwata Wajen lalacewar Tarbiyan Malika kamar yadda Saleem ya Fada...." Ya dakata yana runtse ido wasu kwallah suka zuraromai kafin ya cigaba da Fadin"Sai dai Abu Dayane yamin Yamin ciwo sakin dayayimata kabir,karka manta ko abaya na sanar dakai nayi kwadayin hada zuru"a dakai ne,saboda na samu wanda zai taimakeni ya Tarbiyartar Da malika kan hanya madaidaiciya,Tunda ni na gaza,ya koyar da ita Addinin Allah,wanda zai sa ta rabauta Ranar gobe kiyama,ammh kash saboda Kuskurena yasa Burina bai cika ba..."Yafada yana sakin kuka muryansa ta shake,yana daga kwance. Duk wanda ke dakin sai da yayi kwallah hatta da Ummi da Hajiya babba,sun tsausayama Daddy sosai,Hannu Abbi ya sanya yana Sharema Daddy hawaye yake Fadin"Insha Allahu burinka zai cika kada kadamu Na tabbata yanzu Malika tana matsyin matar Saleem ce,saboda na Turamai sako ta E-mail dinshi na sanar dashi matukar bai Janye sakin dayayima matarsa ba,toh babu shi babu ni har abada,kuma nasan cewa indai yaga sakona zai janye sakin dake tsakaninsu..."yafada yana kallonsa,Saboda Farinciki sai ga Daddy na Hawaye yana mirmishi. Sunjima cikin asibitin sai da zasu tafi suka shiga inda Malika take,lokacin da Hajiya binta ta sanar da ita Iyayen Saleem ne,Sunanshi kawai da"a ambata sai da gabanta ya fadi,lokacin data dago ido ta kalLi Abbi,kawai sai taga yana rikidemata zuwa Fuskar Saleem wacce babu digon tsausayi ko kadan,bayan taja tana makyarkyata,babu inda jikinta baya bari,hawaye kuwa sun Fara wankemata Fuska,Da suka Fahimci hakane yasa basu dade ba,suka musu sallama suka tafi,bayan su ijiye musu Katan katan din lemukan da suka kawo musu,domin dai irinsu Alhaji Abdulmalik baka burgesu don ka basu kudi har gwanda ka basu Abunda kudin ya siya.   ___________________ *CHICAGO* """Kwance yake akan wata kujera,mai kama da goduwa,ammh ba chan ba,ya zuro kafarsa daya kasa,daya kuma ya dorata bisa wani karamin Center table din glass,wanda ke tsakiyar kayatattacen Falon konace tsararre. Sanye yake da wani karamin wando baki 3quater,jikinsa babu riga sai wata farar vest,wacce ta dan kamashi,ammh ba sosai ba,idanuwansa suna lumshe ne,yayin da sanyin gari tare da Dakin yake Fitar da wani Ni"ima na dabam,Duka hannunsa,suna kan kirjina,ya zagaye shi dasu,ammh kana kallon Fuskarsa zaka Fahimci koda barcin yake toh yana matukar jin dadin barcin dayake saboda yadda lokaci bayan lokaci yake sakin mirmishi shi kadai. Ya dade ahakan kafin naga ya bude lumsassaun idanuwansa,kamar wanda akayima duka,ayanayin yadda ya yunkura ya mike zaune,sauke duka kafafunsa yayi bisa lallausan cafet din daya malale Falon,kanshi ya jingina jikin cussion din kujerar,yana shafa sumar kanshi har zuwa fuskarsa kafin ya gangaro zuwa sajensa,da kuma gemunsa,wanda yafara barinshi yana taruwa Shi kadai indan ya Tuna Abun sai yaji tsikar jikinsa ya tashi,yaji gabadaya jikinsa ya saki,kuma kasala ta rufeshi,bayan Faruwar Ramuwar yaji dukkan Nauyi tare da bacin ran daya kunsa shekaru biyar sun Washe daga zuciyarsa,yaji yasamu salama da sa"ida,ammh Abun da bai sani ba shine yau kimanin kwananshi goma da zuwarshi kasar ta Chicago,duk da bai samu zama ba,akwanakin da isa,saboda zirga zirga kammallah sauran abubuwa,da kuma samun muhallin zama,wanda ayanzu yake cikin tsarin wasu apartment,masu kyau da tsari,inda yake sama hawa na biyar. Abunda ke bashi mamaki Shine ko da zai Wuni bai Tuna Abun ba,ammh da zarar yazo kwanciya barci,daya Runtse ido sai Abun yazomai,babu inda ke kashe mai jiki,sai Ni"mar daya kwaasa ajikin Malika,tare da wata Natsuwar da Tunda yake baita samu ba,duk da bai taba sassan jikinta ba,buh he know her body is so softy sexy and Ronantic,wani lokacin in baiyi wasa ba har mafarkin ya kara saduwa da ita yakeyi in ya tashi da safe yayi ta jin haushin kansa,dayayimata zuwa daya cizon yatsa yake aransa yana daya sani yakara Mata koda Second around ne,da Duk haka bai Faru dashi ba Tunani yake yana ayyana ashe haka ma"aurata ke Dibam gara bai sani ba,tsakani ga Allah Tunda kaddara tasa ya dandana,toh fa dole yazo yayima Rayuwarshi Fada,da zarar ya koma gida zai nemi mata yayi aure don tsakani ga Allah Tunda yagane Dadin wajen mawuyacin Abu ne yakara juriyan dayayi Ada,kafin yasan Dadin Abun... Wannan Tunanin ma dayake gabadaya tsigar jikinsa ya tashi,yanayinsa Tuni ya chanza,hannu ya sanya yana Dafe Sandar girmanshi,wacce Ta mike sambal,tana barazanar fasa wando🙈😜Dafeta yayi da karfi yana sakin Nishi sama sama,yadade cikin wannan Halin kafin ya bude idanuwansa da suka chanza kala suka koma jawur. Akasalance ya dago kanshi ya zura hannu ya dauko Syetem dinshi dake gefe ya she ,kan Center table din dake gabanshi ya dorata bayan ya jawo Abun zuwa gabanshi,Budeta yayi yafara latse latsenshi yafi minti talatin kafin ya fara gajiya har zai Rufeta sai kuma ya fasa, Aransa yace bari ya Shiga E-Mail dinshi ya gani ko ambarmai sakonni. Yana shiga ya tarar da sakonnin ba adadi,ammh sako biyu ne sukafi daukan Hankalinshi sakon ya marwan dana Sadiq kamar bazai bude ba,sai ya fara Shiga na Sadiq inda yaga uban ashariyan zagi da tsinuwan da Sadiq ya dinga jeramai,yana fadamai Halin daya jefa mutane,aciki harda halin da Malika da mahaifinta ke ciki,ko ajikinsa yana karantawa yana dariyar jin dadi,domin Tuni sunyi waya da Inspector Sale ya sanar dashi komai,duk da Tun zuwanshi garin sau daya yayi amfani da wayarsa. Bai maidamai da amsa ba ya Fita ya bashi waje yana yar dariya,sakon ya marwan Shi yayi Nadamar Budewa, Da kakkausan kalamai cikin Manyan haruffa yaga sakon Abbi zuwa gareshi,Zufa yaji Ta ko"ina ta zuraromai,hankalinsa in yayi Dubu ya tashi,jikinsa narawa ya fara tafamai da amsa kamar haka. _Don Allah Ya marwan kabama Abbi da Ummi Hakuri,wlh nayi kokarin samun wata hanyar da zanyi Ramuwana,batare da hakan ya shafesu ba,ammh na gaza na samo wata hanya,sai nayi duba naga wannan Shine hanya maafi sauki,don Allah suyi hakuri su Yafemin bazan kara ba,Kuma Wlh na janye sakin danayi mata yanxunan,Ammh don Allah kada kabari Abbi ya cireni daga cikin Sawun ya"yansa,da zarar nagama Abunda yakaini nan da wata 2month da wasu kwanaki zan dawo gida_ Yana gama Rubutamai ya Turamai yana kashe System din gabadaya ransa amatukar bace,wlh inda yasan Abun zai gani kenan bazai taba duba sakon ba,koda yakoma gida sai ya Fake da bai bude sakon Ya marwan Din ba,Tagumi ya zuba yana ayyana irin cutar da akamai,wai ya maida shegiyar yarinyarnan dayafi tsana dakowacce mace,tsaki yaja kafin ya mike yana tafiya kafarsa na nitsewa cikin Cafet din dakin ya nufi wani koridi,jim kadan sai gashi ya Fito dauke da Ruwa ahannunsa yana sha gefe daya kuma yana duba agogon Fatan dake Daure ahannunshi,tsuke bakinshi yayi yana Fadi asarari. "Tunda yarinyarnan ta Shigo gonata ban huta ba,na Rama ammh kuma Kaikayi na neman yakoma kaina...Yazama dole na ninka ramuwa na akanta na ci ubanta dakyau yadda yakamata.." Yake Fada yana dan mirmishi kafin ya Cigaba da kurban Ruwanshi,yana wani Yamutsa Fuska kamar an sashi dole. _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 *Shakira* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Littafin *MALIKA MALIK* Na kudi ne ki biya kudin karatu akan Naira 200kachal👌ki turo ta account Nomba kamar haka 0552179550 *JAMILA UMAR GTB* bayan kin dauki hoton Sreenshoot din Transaction  din,sai ki turomin ta wannan Nombar 09069067488,Ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488 shima kai tsaye bayan an dauki  hoton katin sai aturo*_ ~D last Free page,kamar yadda nayi alqawari so mai bukatar ganin Wannan Kafcen,na tsakanin Saleem da Malika,da kuma ganin salon soyayya cikin Ramuwa,sai ya biya kudin karatu ta Details din dana bada asama,Ina maraba da masoyana Masu son cigabana~   *12*     ""Sati Hudu cur Malika ta kwashe a general hospital tana samun kulawa kafin ta warke sumul abata sallama,shiko Alhaji Abdulmalik sai da yakara sati daya akan na Malika kafin shima sallameshi su rankaya su koma gida. Ba laifin an samu cigaba sosai game da laluranshi,domin sun dorashi kan mgunguna,ga kuma gashin kashin dasukeyimai kullum,shiya taimaka wajen fara motsi da hannushi zuwa kafadanshi,shiyasa suka sakasu suka siya wata wheelChair,wacce daga kasar China ma,akayi odarta,wanda take hade da rimot din sarrafata jikin keken,basai an Tura mutum ba,tana da Abun control dinta ajiki,duk inda mutum yake so yana daga zaune sai ya danna ta kaishi ko"ina yakeso indai acikin gida ne. Koda kafin Asallameshi ya dawo gida Tun yana asibitin Hajiya binta tayi tayi dashi ya bari su Fita dashi waje,ammh Alhaji Abdulmalik yaki bari afita dashi zuwa kasar ketare domin nema mai mgani,yace ta kyaleshi kila haka Allah keson ganinshi,ta kyaleshi kawai baya bukatar aje dashi ko"ina,hadda yan"uwansa ta hadashi,ammh yaki yarda da zencensu Dole suka rabu dashi basu da yarda zasuyi Tunda yaki yarda. Jinyar Nashi sai takoma gida,wajen Hajiya Binta,duk da koda yana asibitin ita keda alhakin kula dashi,duk da kawu Shitu na taimakamata,toh yanzu ya koma gida,saboda hidimar gabansa da kuma iyalansa,joda ce kuma ta koma mkranta duk da yanzu wahalar ta ragu Malika ta warke sai Abunda Ba"a rasa ba na damuwa. Yanzu Malika takoma kamar ba itaba,mgana ma sai yazama dole takeyi,kosu Dose da mery sunga chanji,don yanzu suna gama hadamata Ruwan wanka zata sallemesu,ta shiga tayi da kanta,ita yanzu kunyarma Duniya ta isheta,domin tariga data sani cewa lbrinta,da mummunar gaddararar daya sameta yagama zaga Duniya,shiyasa ko Excorts dinta duk ta sallamesu,Joy da peter kadai ta bari sai su mery da Dose,suma saboda masu kula da hidimarta na yau da kullum ne. Gidan ko Da Alhaji Abdulmalik ya mallakama Saleem ko,sai dai aka bar megadin gidan yana kula dashi,Satin Daddy daya dadawowa gida sai ga Manajojin kamfanoninsa,dana gidan mansa,dake gida Najeria,sun kawo maza ziyarar dubiyi,da kuma tabbatarmai da zasu rike amanar dake hannunsu,sun nemi ganin Malika,ammh kiri kiri taki Fitowa daga daki,dole suka tafi suna masu tsausayama wannan Ahalin ga Dukiya har Dukiya,ammh ta gaza yi musu mganin damuwarsu. Tsakaninnsu kwana biyu sai ga wakilan Hannayen jarinsa na kasashen ketare,mrs Suzan da Mr john Abraham,Sunzo duba jikin Daddy tare da rokon Malika ta dawo su cigaba da huldar kasuwansunsu tare,domin suna jin dadin harka da ita,tun kafin Daddy ya basu amsa Malika ta basu,ta sanar dasu bazai yuyu ba ita yanzu bata da sauran wani motsi ko wani Dubara aduniyarnan,kawai su cigaba da gudanar da komai,ga waya sai su dinga tattaunawa,ammh malika bata ko sha"awar Fita yanzu domin tana ganin Tabbas duk randa tafita sai ta samu masu Nunata suna mata dariya. Ayanzu haka tarage shigar banzanta,ammh bata iya saka kayanmu na hausawa,sai dai ta sanya dogayen Rigana,irin na kamfanin Armani,sai ta saka gyalen doguwar rigarta ta yane kanta dashi,bata cin Abinci sosai,sai in Daddy ya matsata,shiyasa wani lokacin tafi son ta Wuni daki ta kwana bata Fito ba,sai dai in Daddy yagaji da cigiyarta ne sai Hajiya ta leka ta kirata,Abinci ko wani lokacin yadda su Dose suka jera haka zasu so su dauka,sai ta Wuni bata sa komai cikin bakinta,don ita ayanzu tafi kaunar mutuwarta Fiye da komai,don gani take tatashi A malika malik dinta ta koma Malika kawai. Dr Abbas,shine Amintattacen Likitan Su Malika,tun tuni,toh bayan dawowarsu gida shi ya rinka zuwa yana duba Daddy agida duk bayan kwana,shiya sanar dashi ya daina zama adamuwa ya rinka samun abokin hira,yadaina zama shuru,shiyasa yanzu zaka ganshi zaune afalonsa, yayi tagumi shuru shi kadai,Hajiya binta ko wani lokacin take zama,dashi in ko tatafi kichen sai dai ya zauna shi kadai. Ganin haka yasa malika tadinga daurewa tana zama dashi,ammh wani lokacin sai dai yayi ta mganarsa bata cewa uffan,daga eh sai A'a,daya mtsamata da Nasihan tayi hakuri,sai dai kawai yaga tana share kwallar kuka,sai ya kyaleta sai dai ka gansu sunyi zugum,ba mgana shi Alhaji Abdulmalik takaichinsa Daya ko azakar din nan bai iyaba,balle aje ga karatun alqur"ani,balle ya dinga karantawa ko azuciyarsane,shiyasa sai dai ka ganshi yayi zura gwanin ban tsausayi,toh balle ita yarsa tasa,da bata san komai na addini ba. Gabadaya Malika ta tsorata da Abunda Saleem yayimata ko barci take ta dinga mafarkin Abun kenan,haka zata farka tana kamkame jikinta tana Fizge fizge tana bashi hakuri,Sai daga baya ta gano mafarki,kuka kuwa tayishi kamar idonta zai tsiyaye in tatuna yau wai itace bazawara,Abun na mata ciwo sosai,shiyasa suna ko mai harafin S taji an ambata sai ta zabura ta tsorata,balle a ambaci sunan Saleem kai tsaye yanzu zaki ga ta fara makyarkyata tana hawaye,Idanuwanta suna nuna tsoro kara kara,shiyasa ta haddace kaminshi tsab,kamar yadda ko ya Fada Yadda bazata manta Abunda yayi mata ba ,To tana jin har abada batajin zata manta muguwar Fuskar *SALEEM KABIR KUMO* Sai ga Malika,yanzu duk wannan ji da kan da rashin kunyar datakema Hajiya binta bashi,tsakaninta da ita yanzu sai gaisuwa,yau an wayi gari Malika zata kalli Hajiya binta tace mata ina kwana,duk da daga nan bata kara cemata komai,ammh ko ba komai An samu cigaba sosai,haka da Joda tadawo,wlh ganin yadda Malika Takoma sai da tayimata kwallah,ada bata tsausayin Malika ammh dole duk wani mai imani ya tsausayamata,shiyasa itama taji kawai ta tsani ma Saleem gabadaya Tun sanda ya ketama Malika haddi,bana irin yadda addini ya koyarba,sai ta hanyar karfi kamar wani dabba Ita ke zama da ita koda bazasuyi dogowar hira ba,mutum ma rahama ne,kuma Afuskar Malikar zaka Fahimci tana jin dadin zama da joda sosai,haka joda zata dage tayi ta bata lbrin rayuwarsu ABU chika da suka je pratical,itako tana Saurarenta sai dai kawai taga ta murmusa alamar tana jin dadin zama da ita sosai. ___________________ Lokacin da Ya marwan yaga sakon Saleem,tsaki yaja ya Fice ko amsa bai bashi ba,sai dai ya kira Abbi ya sanar dashi Abunda Saleem din yace,yaji dadin hakan duk da bai nunama Marwan din ba,ammh shi ya Fahimci hakan.. Abbi bai yarda al"qawari ba lokaci bayan lokaci yana zuwa ya Duba Daddy,su Wuni suna shan hiransu,wani lokacin in yazo har yatafi baya saka malika a idanuwansa,wani lokacin ne takan Fito su gaisa sama sama ta koma daki gwanin ban tsausayi,Duk da yanzu tana kokarin sallah akan lokaci,sai dai Abunda ta gaza samu wanda zai zaunar da ita ya koyamata addinin da kyau shine bata dashi,sai dai kawai Abunda ta iya takeyi,sallan nata ma ba cikakka takeyi ba,balle in ta idar tana son yin addu"a akan Halin data ke ciki,ammh bata iya ba,sai dai ta zauna tayi zuru tana sharan kwallah,tana fadin aranta Allah ya sakamata kawai. Shiko Saleem,tundaga wannan sakon bai kara turama kowa sako daga gida ba,duk da yaga Ya marwan din ya bude sakonsa,ammh ya Fita batunsa bai bashi amsa ba,bai damu ba dama burinsa sakon ya isa ga Abbi,kada sai ya koma gida Abbi ya batamai rai Fiye da yadda shi ya bata mishi. Shiyasa ya maida hankalinshi kan Abunda ya kaishi yana kokarin yagama komai kafin ya koma gida ya Tunkari Abunda ke gabanshi,domin yasa tabbas,zai Fuskanci barazana daga iyayensa nasa,wadanda suka dauki Fushi dashi sosai akan lamarin Yarinyarnan,koma menene ya Shirya tsab wlh ko da anshashi dole ya zauna da yarinyarnan,Tohpha sai ya kara amfanin da wannan damar domin Ninka ramuwarshi gareta.    ******************* *AFTER 2 MONTH*   Kwance tace bisa makeken gadonta ta dunkule cikin blanket,tana ta rawan sanyi domin kana jin yadda hakoranta ke bugan juna,Tun kwana biyu da suka,wuce takasa gane kanta,kwana take da zazzabi ga tashin zuciya,kuma sometimes tana Fama da taruwar miyau abakinta,ga kasala da yawan Mutuwar jiki,barci ko bata gajiya da yinsa,tarasa wazata fadama damuwarta ne,Ko jiya Da hajiya ta ganta sai da ta tsaya Shuru tana kallonta kafin ta tambayeta meke damunta,yamutsa fuska tayi kafin tace itama bata sani ba,kuri tayimata da ido kafin ta kada kai kawai ta Wuce batace komai ba,ammh cikin ranta gabanta yana bugawa kada Allah sa hasashenta yazama gaskiya. Yau Abun yayi tsanani don dakyar ta iya tashi tayi sallar Asuba,ta koma zazzabin ya rafketa,ganin har karfe 10:00am na safe bata Fito ba,toh a kidanta gari na waye zata Fito taje Falon Abbanta inda yake xaune bisa kekensa ta gaisheshi,su dan taba hira kafin ta koma daki,ammh yau ko Duriyarta baiji ba,shiyasa ya damu yama hajiya binta mganar don Allah ta Dubomai Bby tana lafiya kuwa?.. Ita ta shiga da kanta har dakin nata,ta iske su Dose suna ta gyaran Falon,gaiaheta sukayi ta amsa tana tambayansu ina Malika,nan suke sanar da ita Madam,tun jiya bata Fito ba kada kai tayi,kafin ta tura kofar bedroom din ta shiga da sallama,Sai dai ta dade tsaye tana dube dube kafin ta hango malikar kundundune cikin bargo tana makyarkyata,da hanzari ta karisa gareta tana Fadin"Malika..."Take Fada tana zama kusa da ita, Jin Shuru yasa ta yaye bargon jikinta tana Fadin"Lafiyanki kuwa yau shuru....Ashhh..!Mganarta ta katsene sanda ta taba goshinta taji zafi rau,waigowa Malika tayi tana rike bargon jikinta na rawan Sanyi tace'Banda lafiya ne Hajiya Tun jiya da daddare..."Hajiya binta tace",Wayyo sannu bari naje na sanar da Alhaji dama shi yace na duboki yajiki shuru,ammh ki tashi kiyi wanka ki karya kafin nayima Dr Abbas Waya.."Da kai ta amsa kafin takara dunkulewa cikin bargon. Hajiya binta tadade tsaye tana kallon Malika kafin ta Fice daga bedroom din,Su Dose ta umarta dasu hadama Malika Ruwan wanka itama Merry tace mata ta sauka kasa,taje kichen ta amso breafsat din Malika,awajen Atika da toh suka amsa kafin kowacce Ta nufi inda aka sata. Koda Hajiya binta ta sanar da Daddy hankalinshi ya tashi jikinsa na rawa yace ta kiramai Dr Abbas tace yazo da hanzari Babby ba lafiya, hajiya na sanar dashi yace gayinan ahanya zashi asibiti ammh gashinan zuwa. Tagumi yayi yana Fadin"Haba shiyasata najita shuru,meke damunta ne Binta..? ajiyar zuciya ta sauke kafin tace"Zazzabi ne inaga,don jikinta yayi zafi sosai..."Girgiza kai yayi yana fadin"Binta zuciyata takasa natsuwa taimakamun zuwa dakin Baby don Allah.."Bata yi gaddama ba ,ta isa bayanshi tafara turashi zuwa dakin Malika. Koda suka shiga harta fito wankan,ta shirya cikin wata doguwar riga,ta koma ta kwanta tana nishi,Hajiya ce ta shiga ta rikota suka Fito falo ta kwantar da ita kan kujera,Daddy ya karisa gareta yana kan kekenshi yake fadin"Sannu Babyna..."Dakyar ta dago tana kallonshi hawaye suna gangaromata,bata iya amsawa ba,illah rarrafowa datayi ta kwantar da kanta bisa cinyarsa tana nishi dakyar. Hannu yasa ya dafa kanta yana jin yadda jikinta ya dau zafi sosai,Shafa kanta yake yana jeramata sannu,kafin ya kalli Hajiya binta yana fadin"Binta nace ko zata ci wani abun ne kafin Dr Abbas yazo,kila yace zai maka allura ma.."gyada kai Tayi kafin tayi mgana ma merry dake gefe ta shiga kwaso kulolin data dauko da kasa tana jerawa gaban Alhaji Abdulmalik,wacce malika take kwance kan kafafunsa,rabin jikinta na kasa tana nishi sama sama. Dakyar Daddy ya iya lallabata ta sakeshi ta zauna ta jingina da kujera tana yamutsa fuska,tunda aka bude Ferfesun kayan cikin,taji zuciyarta na tashi,ta kauda kai tana wani toshe hanci,mamaki ya kama Daddy ya kalleta yana Fadin"Bby menene...? Kuka ta fashe dashi kafin tace"Daddylove zuciyata tana tashi adaukemun shi daga gabana,inaji kamar zanyi amai..." Da Sauri ya umarci merry data Rufe kolan kafin ya kalleta yana Fadin"To an dauke yanzu me zaki ci,ta hada miki tea,...? Gyada kai tayi duk da batason cin komai,ammh bata so tabar Daddynta yana zama cikin worry akanta. Tea din ta hadamata ta mikamata cikin wani kofin glass,mai kyau karba tayi tafara kurba ahankali,ko Kurba uku batayi ba tafara jin zuciyarta na tashi,tayi saurin mikama merry Kofin bata kai ga mgana ba,taji Daddy na Fadin"Haba Babby ki daure kisha mana,ga Dr nan zuwa yanzu sha kigani...",tana so tayi mgana Abun takasa saboda yadda madarar ke taso mata,amai taji ya zomata da karfi ko kafin ta mike tafara kelayashi awajen cikin kayan abincin dake gabanta. Daddy yace"Subhannallah..,Binta kamata karta fadi..."Da sauri Hajiya ta karisa tana riketa tare da jeramata sannu,sai da ta amaye dan shayin data sha tas,kafin wani ruwa ruwa ya biyo baya yunkuri take,ammh komai baya Fitowa saboda babu komai acikinta,shiko yana gefe yana jeramata sannu kamar zai mata kwallah Fadi yake"Kai wai ina Dr Abbas ya tsaya ne..? yake Fada cike da damuwa. Sai da tagama kafin tayi baya jikinta babu karfi hawaye suna Fita daga idanuwanta,Saboda yunkurin aman har Fitsari tayi awajen duk ta bata rigar dake jikinta,Kan kujera Hajiya ta kamata ta kwanta tana maida numfashi,su kuma su Dose suka fara kokarin kwashe kololin da ke wajen ita kuma ta dauko Abun goge goge, tafara goge wajen,suna cikin hakane Dr Abbas ya kira wayar Daddy yace gashi awaje. Hajiya binta tasauko taje ta mai jagora har zuwa sama Falon Malika,inda sukayi musabaha da Daddy yana tambayanshi ya jikinsa,amsamai yayi da"Jiki yayi sauki,don Allah Dr Bby zaka dubamin tun jiya take fama da zazzabi,yau da safe kuma jikinta yayi zafi,yanzu haka ka ganta nan amai tagama.." Yafada yana nuna mishi ita,Jinjina kai yayi ya karisa gareta,durkusawa yayi gabanta yayi yana Fadin"Sannu Madam,..."Dakai ta amsa idanuwanta na lumshe,ita kadai tasan halin data ke ciki,kallonta yayi yana nazarinta kafin yace"Plz madam,ko zaki iya tashi,saboda na dubaki da kyau..."jin haka yasa tafara yunkurin tashi da sauri Daddy yace"Don Allah Binta taimakamata..."Yafada yana Tura keken nashi zuwa gaban Malika. Ita ta riketa tatashi zaune bayan ta jingina da cussion din kujera tana maida numfashi,mikewa yayi kafin yadan rankwafa,yasa hannu ya dalle mata ido duka biyun,yana kallo kafin ya saketa,ya koma ya riko duka tafukan hannuwanta yana kallo kafin yace"Arm madam plz yaushe rabonki da ganin period dinki..? Bude ido tayi ahankali tana kallonshi kafin ta bude baki ta kyar tace"2 month kenan,+ dis month shima ban gani ba haryanzu,kuma date dina 16 ne.. "Tafada tana yamutsa fuska. Gyada kai Dr Abbas yayi kafin yace"Is ok bari na Dibe jininki na tafi dashi lab,su auna buh ina kyautata zaton madam u are pregnant..."Gabdayansu suka raazana da jin wannan mganar daga bakin Likitan,Daddy ne ya zaro ido yana kallon Hajiya binta,wacce tayima Malika kuri,domin dama zuciyarta tun shekaran jiya take hasasomata Allah yasa Malikar ba ciki ne da ita ba. Itako Malika tana da kishingide sai gata zaune digigir da kanta idanuwanta duka awaje tana Fadin"Dr Wit pregnant,plz stop dis joke don Allah..."Tafada cikin tashin hankali,da Sauri Dr Abbas yace"No bani da tabbas,buh duk wasu symtoms na masu juna biyu ya bayyana atare dake,so yamzu mu bari har na kai jininki zuwa lab,su auna su gani...."Ya fada yana bude wani karamin akwati daya zo dashi. Siranji ya dauko tare da allura ya hadasu waje daya,ya riko hannunta ya dibi jininta,kafin ya sanya mata auduga ya danne wajen yana jeramata"Srry..Srry...."yana gamawa ya maida komai cikin dan akwatun nashi ya mike yana fadin"in na tashi aiki kafin na wuce gida,zan biyo na kawo muku result din..."Godiya Daddy yayi tamai kafin su sake musabaha ya fice yana Fadin",Allah kara lafiya Madam...." Koda Dr Abbas ya fita ba wanda ya samu zarafin magana,banda shesshekan kukan Malika daya cika dakin,Daddy ko kansa ya sunkuyar yana jin kamar zuciyarsa zata Fito waje saboda yadda take harbawa.,Hajiya binta ko na zaune gefe tana girgiza kai kafin tace"Sai hakuri Alhaji,ammh tabbas ko ni naga alamun Shigan karamin ciki atare da malika,bandai yi mgana bane saboda ban tabbtar ba...." Dagowa Yayi idanuwansa jawur yana fadin"Ciki kuma binta,innalillahi ina Bby zata kai ciki awannan halin datake ciki..."Yafada yana kallonta,gyada kai hajiya binta tayi tana Fadin"Haihuwanshi zatayi Alhaji,toh zamu zubar da Abunda yake da shakikin mahaifi na sunnah,ai da an tabbatar da cikin ka kira Kabir kumo ka sanar dashi Abunda ke Faruwa,nasan suma bazasu ki karbanshi ba,tunda dansu ya digashi..." Ajiyar zuciya ya sauke yana jinjina kai alamun gamsuwa da mganarta,kawai basu ankara suka ga Malika ta mike tana tsalle bisa kujera tana dukan cikinta tana kuka da ihu kamar wata mahaukaciya tana fadin"Bani son wlh bazan haihu ba,zan kashe kaina wlh..."Take fada tana buga jikinta da duka hannuwanta biyu tana kuma tsalle atare..... Da hajiya binta Da Daddy dake kan keke ba"a san wanda ya riga wani ba,shidai Daddy ji yayi kafarshi na rawa kokarin mikewa yake ammh yakasa saboda yanayin jikinsa komawa yayi ya lafe bisa keken yana Fadin"Binta taimakeni ki riketa kada tama kanta ta lahani, Wayyo Allah!...? yafada wasu kwallah na zuraromai,... Dakyar Hajiya binta ta riketa,rumgumeta tayi tana kuka mai cin rai take fadin"Hajiya ya zanyi...? me zanyi kuma? Hajiya ki sanar dani wata addu"a akeyi mutum ya mutu ya huta da wannan Duniya da babu komai cikinta sai bakinciki,..."Take fada tana kamkameta cike da tashin hankali, Rumgumeta hajiya binta tayi wani tsausayinta na Tsirgamata tace!"Ki daina Fadin Haka,babu wata addu"ar mutuwa aduniya sai dai Addu"ar da in wani bala"i ya kusanto ka sai ka karanta,ki maida kukanki ga Allah Malika,don bazaki iya chanza kaddaranki ba,kiyi ta karanta *INNALILLLAHI WA"INNA ALAIHIRRAJU'UN*...Insha Allahu zakiji sauki azuciyarki..." Ahankali ta shiga maimata kalmar asarari,tanayi tana zubar kwallah,Hakama Daddy dake gefe shima tayata maimatawa yake yana sharan kwallahn shima,Malika ne ta kalleshi taga yana kuka,saboda tsausayinshi da kaunarshi bata san sadda ta saki hajiya ba,tatafi gareshi ta fada jikinsa tana kuka harda sheshaheka tana Fadin"Am srry Daddy,plz stop carrying,i love u, i dont want to lose u....." Take Fada tana zame kanta bisa cinyarsa tana kuka da duka karfinta,Kanta yake shafawa har zuwa bayanta,hawayensa suna gangarowa zuwa Kanta yake Fadin"Nabari Babby,ammh nima ki taimakeni kada ki kashe kanki,in kika aikata haka wlh zan zama gafaalle,aduniya kuma asararre aranar gobe kiyama..."Damke hannunshi tayi tana Fadin"Am wit u Forever and every Single day of Forever Daddylove,plz Forgive me...."Take fada muryanta ciikin kuka. Hawaye yake share mata itama tana sharemai,Hajiya binta dake tsaye gefe,itama kwallar ta share tana jin kamar tayima Malika da Alhaji kuka mai yawa,yau din da suka bata tsausayi Fiye dana kullum. _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 *Janafty(Momyn ladingo)* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200👌 ta wannan account 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb din,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,Bazan muku Allah ya isa ba,ga wanda ya karanta bai biya ba,sai dai zan bar mutum da mai Duka wanda ke sama yanan nan madakata_ *KURIKE GIRMAN AMANAR DANA BAKU,KUYI MIN ADALCI KAMAR YADDA NAYI MUKU KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*👏 *13*        ""A daren Ranar Dr Abbas,ya kawo sakamakon gwajin Malika inda sakamakon ya nuna Malika tana dauke da ciki har na tsawon Sati goma,wato wata biyu da sati biyu kenan, malika ta karbi takardan ta Tsurama ido,sai taji kwallah na zuraromta,lokaci daya dawani takwalli da kuma natsuwar zuciya Tun bayan data dinga maimaita Innalillahi wa"inna Alaihirraju'un,kawai don kuka ya zama dole ne gareta,ammh lokaci daya tana jin tana bukatar itama abokin da zai kasance shi kadai ne zaiji kanta Aduniya,shiyasa ta daura kudirin kullah kawance da Abunda ke cikinta,kila watarana shi zai zama gatanta. Hankalin Daddy ya bala"in kwanciya lokacin daya ga Malika ta kwantar da hankali,bata kara nuna damuwarta kan cikin ba,Dr Abbas da kanshi ya kawo mata magungunar karin jini,da kuma na sa cin abinci,yawan tarun miyau kuma datakeyi,ya umarce ta data rika yawan shan sweet hakan zai taimaka ya rage tsinka mata yawu. Mganar Amai kuma yace sai zuwa cikinta in yayi kwari,ammh yace taguji Abunda bataso,saboda shima yawan aman yana sakarma damai ciki jiki,duk sai tazama ba kuzari atare da ita,wani lokacin ma sai anyi mata taimako da drip ko zata samu karfi,ta karbi duka dokokin likita da hannu biyu kuma ta shiga kokarin kiyayewa,Sai dai Abun da bata gane ba Hajiya binta ta taimakamata. Sai washegari kana Daddy ya kira Abbi ya sanar dashi Abunda ke Faruwa, Abbi na zaune bisa kujera afalonsa Ummi na gefensa alokacin,Mikewa yayi Tsaye yana Fadin"Allahu Akbar..!Allahu Akbar..!Allahu akbar..."!Har sau uku yana nanatawa kafin yace"Kaji ikon Allah ko Abdulmalik,Wlh rabon dake tsakaninsu ne yasa akayi auren nan cikin gaggawa,da"ace munyi tsaiko ko munyi gaddama toh da Allah ya nuna mana karfin rabo,ko wani cikinmu ya bar Duniya,ko asamu cikin ta wata hanya,wanda dukkanmu bazai mana dadi ba,Kai Allahamdulillahi Allah Abun godiya,ina malikar tana lafiya ko? Yafada yana bayyana Farincikinsa Amganarsa. Daddy yana mirmishi yake Fadin"Hakane wlh Abokina,sai mu godema Allah,Malika na nan lafiya,sai dai Abunda ba"a rasa ba,kasan masu shigar sabon ciki sai ahankali,wuni take amai komai taci sai ta dawo dashi,abincin ma ba sosai take ci ba..."Jinjina kai Abbi yayi kafin yace"Allah sarki hakane Abun sai ahankali agaisheta kafin muzo,kuma insha Allahu mijinta nadawo zai zo ya dauki matarsa ya kuma baku hakuri insha Allahu. Daddy yace"Ayyah bakomai kumo,Allah dai ya Rufamana Asiri kawai.."Nan suka Cigaba da tattaunawa kafin su yanke kiran,Ummi dake gefe ta zaku ya gama wayar taji wani Abun Farinciki ne ya samu haka,yake ta faman washe baki yana kabbara. Nan yake sanar da ita Abunda Daddy ya sanar dashi,Washe baki tayi tana hamdala ga ubangiji take Fadin"Masha Allahu da samun Surikar Farko,kuma Alhamdulillah da samun karuwar jika agidanan akaron Farko..."Take Fada duka hakoranta waje,Mikewa tayi tana Fadin"Bazan ji wannan Abun Farincikin ni kadai ba,dole sai Hajiya taji itama.."Ta fice yana mata tsiyan ko kunya,itako tana Fadin"Ba marwan bane,saleem ne ba Dan Fari bane balle yace wani Abu.." Da Hajiya Babba Taji rike Ummi tayi tana Fadin"Don girman Allah Da gaske kike Aisha...? Tafada tana zaro ido,Rantse mata tayi tana sanar da ita shi mahafin malikan da kanshi ya kira waya ya sanar da Abbi,ai Hajiya Sakin Kabbara tayi itama kafin tace"Kai Salihu Dan albarka ne,da haushinsa nakeji game da ta"asar da yayi ammh yanzu ya wankemun zuciyata kal,kai ni wlh duk gidan nan ko Kabiru yanzu bai kai Saleem Farantamin ba,shi yafara yin aure agidan nan,gashi kuma shi zai Fara haifamin tattaba kunnina ina raye..."Tafada tana sharan kwallah Farinciki,lbri fa ya zaga ko"ina hatta Saleema dake mkranta tasamu lbrin nan,wanda Sadiq yake sanar da ita,shima Ummi ta gayamai shiko Marwan yana chan ya samu lbri jinjina kai kawai yayi yana Kiyasta dama ana samun ciki daga zuwa daya😝🤔,lalle ko in hakane ya jinjinama Karfin mazankutan kanin nasa.   ******************* Jirgin daya kwaso al'ummah Dabam Dabam daga birnin na ikko wato lagos shine ya yada zango A babban Filin jirgin Mallam Aminu kano international Airport. Acikin wanda jirgin ya sauke harda Acp Saleem kabir kumo,wanda ya sauka jiya da daddare,daga kasar ta chicago,to dama dayake jirgin daya shigo wanda zai yada zango a lagos ne,shiyasa ya kwana a hotel da safe kuma ya biyo jirgi zuwa kano. Tafe yake wayarsa makale akunnasa yana sanar da Inspector sale,gayinnan karisowa,sanye da riga da wando black and White,na kamfanin armani,sai wata jaket daya dora asaman farar rigarsa,jakar brief case dinsa ne makale ne kafadansa,sai kafarsa dake sanye da Rufaffen Takalmi na Fatan damisa. Hankalinsa na kan wayar da yake yi sai ji yayi gam!an ban gaje shi yayi baya har sai da wayar hannunsa ta subuce masa ta fadi kasa ta tawartse, dagowa yayi cikin zafin nama yaga wani banzan ne,wanda ke Tafiya baya kallon gabansa. Ita kuma ta taho tana sauri hankalinta yana ga Best dinta tada hango,hannu ta dagamata jikin ta na rawa ta nufeta,ashe shi kuma saleem ya taho,kawai sai ta bangajeshi batare dama ta lura ba,sai da mai afkuwa ta Faru. Durkushewa tayi tana tararra mai wayar tana Fadin"Oh! my god...Na bani ni Zahra..."Take Fada tana kwaso mai part part din wayarsa data baje akasa,Dagowa tayi daga tsugunnan ta mikamai wayar tana Fadin"Am so srry  I don"t know dat u ar coming kayi hakuri..."Ta fada lokacin data sanya idanuwanta akansa bata san sadda ta Furta "Wow...!!!..."Saboda yadda gayen ya Tafi da duka imaninta. Shiko sagale yayi yana binta da kallo,kyakyawan Budurwace,doguwa mai kyan tsari da jiki dana Fuska,fara tas,ammh daga kallon Farko zaka Fahimci tana da rawan kai da kaudi,Sanye take da riga da sikat na wani leshi mai adon duwatsu,ta sanya babban mayafi ta Rufe jikinta,cikin Abunda baifi sakan goma ba,ya kare mata kallo,itako bakinta sake tana binshi da kallon kurillah zuciyarta na bugawa. Yaken baki yayi mata kafin ya mika hannu yana fadin"Is ok..."Ya fada yana mikamata hannu da nufin ta bashi wayarshi,gani yayi hankalinta baya jikinta ta saki gabadaya hankalinta akanshi tana kallonshi,wani takaichi ya cikashi,da dan karfi ya Furta"Hy..." Sai gashi tayi Firgigit ta dawo hayyacinta,bai mata mgana ba,illah hannun daya mika mata,kunya duk ta kamata tana sosa keya ta mikamata tana fadin"Tanque sir..."Kanzil bai ce mata ya ratsa ta gefenta zai Wuce ganin da gaske yake tafiyan zai yi yasa da azama tace"plz Nace ba...?. Cak ya tsaya kafin ya waiwayo yana Fadin"U say what...? Mirmishi ta sakamai kafin ta mikamai farin hannunta tana fadin"Am *ZAHRA BUKAR MADA* by Name, inko...? Wani kallo ya watsa mata kafin ya dan ciza gefen bakinshi yace" Am *ACP SALEEM FREEKING KABIR KUMO*..."Da hanzari ta katseshi tana Fadin"Wow Fabulos,ashe ina tare da ACP ne,kai Nice to meet u Sir..." Mirmishi yayi mata,ganin yadda take wani rawan kafa,yana shirin barin wajen takara cewa"Plz sir can i hv ur digit...? Zaro ido yayi yana fadin"Whta...? Langwaba kai tayi tana Fadin"Plz Sir...,? Bata rai yayi saboda tsakani ga Allah ta isheshi agogon hannunsa ya duba kafin yace"Ok 080.......'"😝Haka ya rattabamata tana kwashewa bisa wata faskekiyar wayarta kafin ta gama tana Fadin"Tanque Sir..." Juyawa yayi yana Fadin"U ar wlcom..."Da kallon sha"awa ta bishi ganin yadda yake takunsa cikin isa da takama,tana kallonsa har suka hadu da inspector sale,suka yi musabaha suka gaisa,kafin su danyi wani mgana,suka kara musabaha,kafin ya bashi key din motarshi sukayi Sallama daganan shikuma ya Fada motarsa kirar 4matic ya Fice daga Airport din da hanzari. Hankalinta na wajensa sam bataji karosowar mutum akusa da ita ba sai ji tayi an daka mata duka abaya,Zabura tayi zata saka ihu sai ganin *BEST NADIRA*  Dinta wacce ke tsaye jaye da Trolly dinta tana zabgamata harara,da hanzari ta Fada jikinta tana Fadin"Wlcm home my best,kefa nake ta jira tun dazu..". Wacce aka kira da best ta bamberata daga jikinta tana Fadin"Toh tsarani,kika dai tsaya tsinannan rawan kanki,keda wa nake hango ki tsaye tun saukowata daga jirgi..? wani Fari ta mata kafin ta ja hannunta da hannu daya dayan kuma taja trolly dinta tana Fadin"Kedai bari my best today i meet my mr Right wlh..."Da kallon mamaki Best din ta bita kafin tace"Topha wanene shi..? Suna tafiya ta bata amsa da cewa" * ACP SALEEM KABIR KUMO*...."Baya taja tana maimata sunan da sigan tambaya"Acp saleem kabir kumo fa kika ce? tsayawa tayi itama tana kallonta kafin tace"eh kinsan shi ne...? Mirmishi ta saki kafin tayi gaba tana Fadin"Eh mana waye baisan shi ba yaron IGP ne fa nakasa gabadaya..."Ido  Zahra ta zaro tana Fadin"Wow!Kice Abba ma zai sanshi...? Tsaki taja tana Fadin"Kina da mtsala,toh bama Abbah ba,kowa dake kasar nan yasanshi,ko kin manta shine fa kwanaki ya auri diyar dan kasuwan nan mai kudin bala"in nan Malika malik,kuma ya saketa adaren Auren.."Kwalalo mata ido tayi daidai lokacin da suka iso bakin motar da zahra tazo da ita kirar 306 tana Fadin"Kai don Allah ya"akayi ni ban sani ba..? Tsaki taja tana zagayawa bangaren mai zaman banza,sai da ta bude motar ta shiga kafin itama zahra ta bude baya ta jefa Torolly din ta bude bangaren Direba ta shigo daidai lokacin da Nadira take Fadin"Dallah wake ta sha"aninki keda sai kiyi sati baki hau social media ba,mu gani kamar last 3 month ne Abun ya faru,wlh kwanakin kowata jarida Abunda tayi ta bugawa kenan haka Social media anyi ta yama didi da zencen.." Shuru zahra tayi bayan tayi Tagumi take Fadin"Toh kuma wai da gaske ne.."?Hararanta tayi tana Fadin" Bansani ba,Tunda zan miki krya ne,Kinga zaki tukamu zuwa gida ne,ko kuwa zaki tsaya jin gaskiyan ne..? Tafada cike da kosawa,tabe baki tayi tana fadin"Oho miki dai,badai ya saketa ba,niko naji na gani inaso,don ganin farko naji yamin wlh best ya sace zuciyata inaji kamar i can't do Withount him..."Galala Nadira ke kallonta kafin ta kada kai tana Fadin"Eh naga alama.."Ta fada tana binta da kallon mamaki,yadda take driving tana mirmishi ita kadai.   *WACECE ZAHRA BUKAR MADA* Diyace ga Tsohon Alkalin Alkalai na kasa gabadaya *BUKAR MADA* Asalinshi dan Maiduguri ne,dagashi har matarshi *HAJIYA SAHURA* Kafin zuwanshi wannan mtsayin ya rike alkalai akotuna dadama kafin yazama Alkalin Alkalai. Sun dade da aure kafin Allah ya basu Haihuwa Mace *ZAHRA* Kuma Tunda ga ita bai kara samun haihuwa ba,gashi da son ya"ya wannan Dalilin ne bayan rasuwar dan"uwanshi Shehu dake lagos da zama shida matarshi da yaranshi,ya dauko Biyu daga ciki, *NADIRA* da *NADIR* wanda ya rikesu tun suna yara awajensa sukayi karatu,har zuwa girmansu.... Ita kuma Nadira da Zahra kusan sa"annin ne tare suka tashi sun Shaku da juna matuka,komai nasu tare sukeyi kamar wasu yan biyu,shiyasa suke kiran juna *BEST*,tare sukayi karatunsu a jami"ar Base dake Abuja,Nadira ta karanta Microbiology,sai Zahra data karanta *Mass com* Dukkansu sun kammallah harta master dinsu kowacce ta gama,ammh basa aiki saboda Abbansu bayi da sha'awan haka sai dai yafi sha'awar kowacce taje dakinta in mijinta ya yarjemata ta yi aikinta,in kuma ya hana ta dai samu ilimin,shiko Nadir likita ne ajami"ar Malesiya yayi karatun likitansa,abangaren mata,ayanzu haka yana Asibitin Mallam Aminu kano yana aiki a matsayin babban likita. Ko atasowar Nadira da Zahra akwai bambamci hallaya atare dasu,domin Nadira tafi zahra wayau da sanin kan Duniya sosai,sakamakon ita Zahra bata son komai sai tabara da sangarta,ga rawan kai da Feleke barta da son asani da kuma Shigen Shisshigi ammh fa sakaryace,sai dai akwai daukan wanka bata shigar banza,saboda Bukar mada bai barsu haka ba,Shida Hajiya sahura basu yi musu Rikon wasa ba, Zahra sha"anin Shigen shigen Yanar gizo bai dameta,ko waya ma ba damunta yayi ba ita dai barta da kallon India Series kamar wata mayyah,to anan tafi Auki,ta Wuni tana kallo bata gaji ba,in ko ka ganta da waya toh ba chart take ba,sai dai game don anan Tafi auki,sakamakon Nadira mace ce mai son Nuna ita wayayyiyace,Tana son Shiga yanar gizo,babu Kalan Social media Da batayi sai dai wanda bai Fito ba,kuma babu Wanda indai ubanshi kusa ne agwannati da bata sanshi ba,shiyasa tasan lbrin Saleem da Malika,domin Malikar ma tana Following dinta a intergram dinta,ada suna zaune Abuja ne,ammh bayan saukan Bukar mada daga Kujerar Alkalin Alkalai,sai suka koma kano da zama. Haduwarta da Saleem A Airport ma taje dauko Best Nadira ne,wacce taje lagos wajen mamanta Hutu,shine suka hadu da Saleem kuma lokaci daya taji ya sace mata Zuciya da gangar jiki gabadaya. Wannan kenan.   _____________________ Shiko Saleem daganan Kano Zamfara ya Wuce kai tsaye,bai fara isa gidansa ba,sai da ya biya headquater su yayi Report ya gaisa da abokan aiyukansa,kafin ya isa gida,yayi wanka yaci abinci dama already ya tsaya wani restaurant ya yi ma kanshi take away,yana gamawa ya fadi bisa gado yana barcin gajiya wanda bai tashi ba sai gab da kiran sallar mangariba. Washegari Tun karfe 7:30am na safe yasaka hancin motarsa bisa hanyar Abuja,domin ya kosa yaje ayi wacce za"ayi domin yasan Abbi da Ummi suna jiracesa dashi ne. A yau din yana sanye ne da Riga da wando,Wandon Nevy blue ne,sai Rigar Ash ce tana da ratsin layin blue ajikinta,kuma dogon hannu gareta,mai dauke da botura ta kasan hannun,kafarsa ko Yau Budadden Takalminsa ne mai kalan blue shima mai kyau da tsari. Kusan mutumin naku da gudu bisa hanya kamar zai tashi sama,sai gashi koda karfe 11:00am na safe tayi mai kofar Tamkamemen gidansu yana Zuba hon,megadi yana lekowa ya ganshi,jikinsa na rawa ya wangalemai get yana mai sannu da zuwa,Shiyama budemai kofar motar sanda ya gama daidaita zamanta a parking space.... Bayan ya Fito sun gaisa kai tsaye ya nufi cikin babban Falon gidan,ammh wani sashe na zuciyarsa na bugawa da tsoro baisan da wani tarba Abbi zai karbeshi ba,da siririyar sallama ya kutsa kai Falon,babu kowa sai karan tashin Talabijin daya keyi Shi kadai,tsaye yayi atsakiyar Falon yana karema ko"ina kallo,ganin babu motsin kowa shiyasa ya kara daga murya yana sallama cikin fargaba..... Ummi na kichen tana hadama Abbi breafsat dinshi yau ya tashi bayajin dadin jikinsa,.taji sallama daga farko,ammh jin Shuru ba"a karayi ba yasa tabasar,ammh sai takaraji an sakeyi bata dauki murya ba ,ta Fito da hanzari tana amsawa sai ta ci karo da Saleem tsaye yana kallonta, Daure Fuska tayi kamar bata taba saninshi ba ballantama ganinshi tace"Lafiya mallam daga ina..? Gwiwanshi ne yaji yayi sanyi yana neman dukawa ya gaisheta yaji Muryan Abbi da kakkausan murya yana Fadin"Kai...Kul!...Kada ka sake ka dukamin Agidana..." Abbi ya Fada yana saukowa daga saman Step sanye da bakar jallabiya,Jin haka yasa Saleem bai dukaba ya mike yana marairaicewa Abbi yana gama saukowa ya kalli saleem yace cikin kakkausan murya "Yi baya nace...!Ya fada da tsawa,sororo Saleem yayi kafin ya bude baki yace"Ab....!Yi baya nace Saleem..!Abbi ya kateshi yana sake maimata mganarsa,mganar Abbi cikin fada ne yasa Hajiya Fitowa tana Fadin lafiya,sai kuma ta ci karo da Saleem baki ta kama tana Fadin"Kai kuma Salihu daga ina haka? sai kace wanda yayi sata aka biyoshi kana wani rarraba ido kamar wani maye..."Tafada fuskarta ba Fara"a Yana ganinta yafara taku zuwa gareta yana Fadin"Yauwa hajiya don..."Saleem zanci mutumcika nace kayi baya kaficemin daga gida ko? Cak ya tsaya yana kallon Abbi shiko kara tamke Fuska yayi yana Fadin"Ficemin daga gidana,ai kaji sakona wlh tallahi indai ni kabiru ni na haifeka bazan yadda kacigaba da amsa sunana amtsayin sunan mahaifinka ba,sai ka juya daganan katafi katsina ,kaje kabama Mahaifin Malika hakura ka kuma dauko matarka ku dawo cikin gidan nan tare,na ganka ka Shigo kafarka kafarta,sannan zan yarda ka sake shigomin gida har ka rabi suna na amtsayina na mahaifinka,in kuma ba haka ba,Wlh tallahi bani ba ka Saleem har Abada kuwa kajima na rantse.... Yana gama fadar haka ya juya yana Fadin"Aisha kawomin Ruwan zafin.."Daga haka ya haura sama ransa bace,toh Ummi tace bata ko kara kallon Saleem ba ta koma kichen ta dauko Fulas din ruwan zafi da kofi tayi hayewarta sama,Hajiya babba ma kallonsa tayi kafin ma tayi mgana taga ya juya Fuu..!ya Fice kamar zai tashi sama baki ta rike tana fadi afili... "Anya wai yaron nan kalau yake...? kai ban yarda ba kila dai ya fara shan kwayoyin zamani..."Tafada tana kara rike Haba, kafin ta juya ta koma dakinta tana sababi ita kadai. Ayi hakuri Typing errors am too busy bansamu lokacin tantancewa ba *Shakira*   *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *Ki biya ki karanta cikin Salama,akan 200👌Akan Account Nomba, 0552179550 JAMILA UMAR Gtb,ko kuma Katin Mtn ta wannan nombar 09069067488* _Wannan page din ya zama Free page ga kowa da kowa,sakamakom samun wata baiwar Allah masoyiyar kwarai gareni daku gabadaya data sanya zunzurtun kudi ta Siya wannan page din tace ayadashi ako'ina,kuma kowa ya karanta,hakika baka iya ganin masoyinka na gaskiya sai hakan ya Faru dakai,wlh tallahi dalilin Rubuta Novel din *MALIKA MALIK* na hadu da masoyana Wadanda banta  zato ba,balle tsammani babu Abunda zence ga Allah sai godiya garesa domin da kudiransa komai ke Faruwa,Ina rokon don Allah duk wanda ya karanta wannan page din ya sanya *MY BEST HALIMATU* Cikin addu'anku,Tare da fatan Allah yayi mata sakayyah da gidan Aljannah Firdausi Ameen_ _* I love u so very much from d bottom of my hrt, may Allah shower his blessing upon u, u are indeed more than a frnd but sister love u...MY BEST HALIMATU*_😍😘 *14* ....................Koda ya Fita Fuu,haka ya Bude motarsa ya fada yana sauke Numfashi,sama sama jingina kansa yayi da jikin kujeran motana yana sakin wani Huci mai zafi,kansa yafarawa shafawa zuwa sumar sajensa,lokaci daya yana tsigen gemunsa wanda ya fara taruwa,duka idanuwansa suna Rufene Ya dade ahaka kafin ya bude idanuwansa yana cija lips dinshi na kasa,Abunda yafimai bakinciki shine cewar da Abbi yayi wai yaje yabama Malika hakuri? to uwarta yayi mata da zai bata hakuri? Shi ba"a ce ta duka har kasa ta bashi hakuri ba,sai shine za"ace ya bata hakuri,Durun uwa ne ma..? yafada yana sakin wani dogon tsaki kafin ya gyara zamanshi yana kokarin Daura Set belt yake fadi abayyane. "Zanje dai na taho da ita kamar yadda Abbi ya bukata,ammh mganar bata hakuri wlh Uwarta bata haifeta bama,wacce zan ba hakurin gaskiya.."Yake Fada yana kunna motar nashi Afusace yayi mata kwana kafin ya shiga sakarma megadin hon ba sassautaawa kamar zai cirema mutane kunni,koda ya budemai get din a guje ya Fice yana kara sakarma motar Speend kyace zai tashi sama ne. Ransa amatukar bace yake kwarara gudu bisa Kwalta,yadda zuciyarsa ke tafasa haka yake tuka motar,cikin abunda baifi awa uku ba,sai gashi yana zuba hon makeken get din gidansu Malika,koda aka wangalemai get din afusace ya danna kai gidan,har yana kusa takema megadin yatsun kafa,da kallon mamaki yabi motar sanda take gyara parking. Sai da ya daidata kanshi kana ya Fito daga motan,ammh Fuskarsa tamau babu alamun Fara"a ko kadan,Megadin ya, ya Fito da hannu,wanda dama yake tsaye yana kallonshi cike da tsoro,jikinsa na rawa yazo yana Fadin"Brka da zuwa yallabai.."giransa ya hade yana Fadin"Ka shiga ciki kace ana mgana da mai gidan.."Kallon mamaki megadin ya bishi dashi,yana so yace mai ai Alhaji baya da lafiya bai Tafiya yanzu,ammh yanayin Saleem din yasa dole ya Wuce sumu sumu jikinsa na rawa. Megadi Hajiya binta ya sanarma da sakon,wacce ta kalleshi cike da mamaki tana Fadin"Waye shikuwa..? baisan Alhaji baida lafiya bane.."Yace"ina ga hajiya...!" Tabe baki tayi tana Fadin"koma waye sanar dashi ya shigo ciki Alhaji baida lafiyan da zai Fito ya sameshi.."Jikinsa na rawa ya Fice da hanzari,koda yazo ya iske saleem jingine jikin motarsa yana faman latse latsen waya,rankwafawa yayi yana Fadin"Yallabai hajiya tace ka shigo ciki,don Alhaji kam bai da lafiyan da zai Fito ya sameka.."Sai alokacin ya tuna ance fa Alhaji Abdulmalik ya samu shanye barin jiki,Basarwa yayi kafin ya wuce kai tsaye bayan ya tusa wayarsa cikin aljihu lokaci daya yana Tura duka hannuwan nasa,cikin aljihun cikin takunsa na isa da takama ya nufi kofar da zata sadashi da babban Falon gidan. Da sallama ya shiga Falon lokacin da wani sanyi hade da kamshi ya dakeshi,ga taushin wani shigen grass cafet dake malale afalon,Tabe baki yayi yana bin Falon da kallo,nan ya cikaro da taftafkan hotunan Malika akowani kusurwa na bangon Falon,Yatsine yake kallonsu kafin yay tsaki aransa yana kara jin tsanarta,Yana nan tsaye sai yaji motsin Ana saukowa daga saman Bene,Dama aleeady yabama Steps din baya ne,so sai ya waiwayo daidai lokacin da Hajiya binta ta karisa Saukowa,idonta karaf akanshi tana karemai kallo. Duk da sau daya Tak ta ganshi,ammh ta shaidai shi,shiko ganin yadda ta kureshi da ido ne yasa,ya dan rankwafa yana Fadin"Ina yini hajiya..."Ta amsa da "Lafiya lau,sannu da zuwa,kamar Saleem ko? mijin Malika.."Wani haushine ya kamashi,nan da nan ya hade giransa kafin ya dan saki yake yana Fadin"Eh..."Daga haka ya tsuke bakinsa,yana kallon gefe. Baki ta washe tana Fadin"Ah!Masha Allah sannu da zuwa yaushe ka dawo,domin kamar naji ana zencen baka kasar ko.? Fuskarsa ba Fara"a yace"Eh wlh jiya na dawo.."Juyawa tayi tana Fadin"Allah sarki,biyo muje Alhajin yana sama ne.."Tafada tana Taka Step,shima ya bi bayanta yana zabgamata harara sai kace ita ta kirashi Dole. Suna shiga Falon sama,inda Daddy yake zaune kan kekenshi yayi Shuru yana Tunanin Rayuwa,Sai yaji hajiya binta ta Shigo tana Fadin"Alhaji kayi bako.."Waiwayowa yayi yana Fadin"Bako kuma..? Ya fada da sigan Tambaya,Eh tace kafin ta cigaba da cewa"Saleem ne Mijin malika..."Tafada daidai lokacin da yake saka kanshi cikin dakin bayan ya cire takalminsa. jin Abunda Hajiya binta ta Fadane yasa Daddy ya washe bakinsa duka yana Fadin"Masha Allahu...."Yake Fada sanda Saleem ya kariso  gareshi shikuma ya danna Abun tafiya da keken atare suka tarbi juna,Saleem yayi saurin yin kasa yana bin Daddy da kallo,ganin yadda lokaci daya y koma kamar wanda ya Shekara yana ciwo. Hannayensu sarke ana juna Daddy yake Fadin"Saleem sannu da zuwa,yaushe ka dawo kasar,don Kumo ya sanar dani daga wajen aikinku an turaka wani karatu ko..."?Kan Saleem na kasa kunya duk ta kamashi,bai taba zaton wannan karban mahaifin Malika zai mai ba,sai gashi yaga sabanin Tunaninshi,Kasa hada ido yayi dashi kansa na kasa ya Furta.."Eh Daddy jiya na dawo.."Daddy yace"Masha Allah,an samo Abunda akaje nema ko.."?Kara sadda kai yayi yana Fadin"Insha Allahu Daddy..." Gyada kai yayi kafin yace"Allah ya bada nasara,ya kuma dafa maka..."Kasa amsawa yayi da Ameen,saboda nauyi da nadama,yana jin zuciyarsa na kara Rauni,kafafun  Daddy yake kallo,yana Tuna sanda yazo da kafarshi ammh yau sai gashi zaune baya iya takawa ko nan da chan,Wani imane yakara kamashi,yana Tunanin iyaye irin Daddy sun kare,wanda za'a yima yarka wannan Cin zarafin da tozarcin,ammh kuma ka hadu da wanda ya aikatama haka,kuma ka karbeshi da duka hannuwaka..? Lalle yaji kamar ya maida hannun agogo baya. Daddy ne ya kalli Hajiya Binta yana Fadin"Binta samomai Abun shama,kinsa fa ya yo Tafiya.."Gyada kai tayi zata Fice yayi saurin cewa"A"a Daddy abarshi bana jin kishi..."Girgiza kai Daddy yayi kafin yace"A"a kar muyi haka dakai,kafa sha hanya,dole kana bukatar Ruwa,maza binta kawomai don Allah..."Da hanzari ko ta Fice,shiko saleem duk ya kasa sakin jikinsa,ballema ya dago kanshi Daddy ne ya kalleshi yakuma karanci yanayinsa mirmishi kawai yayi kafin yace"Ya ka barosu Abbanka,ya kuma su Hajiya da Umminka..? Kansa na kasa yace"Duk suna gaisheku.."Ya amsa da "Muna amsawa...." Daga haka Shuri ya biyo baya har Hajiya ta dawo dauke da tire shake da kayan sanyi,ta jiye agabanshi kafin ta sake Ficewa,Hannunsa Daddy ya saki yana Fadin"Sha ko Ruwane Saleem ka jika makoshi..."Baiyi gaddama ya dauki roban swan mai sanyi ya Tsiyaya akofi yana sha kadan kafin ya ijiye yana sauke ajiyar zuciya,so yake yayi mgana ammh kunya da Nauyin Daddy sun hanasa wani motsi. Gajiya yayi da sadda kai,ya dago yana kallon Daddy kafin yace"Armm Daddy dama Dalilin zuwana Abu daya ne zuwa biyu,na farko domin na baka Hakuri bisa Abunda ya faru,don Allah Daddy kada ka rikeni ka yafemin ajizanci ne na Dan Adam,da kuma sharrin Shedan sai na biyu don na sanar dakai na dade da maida Malika amtsayin matata,yanzu haka nazo neman izininka ne zan tafi da ita,muje mu zauna muyi zaman Aure na hakika.." Har ya gama mganarsa Daddy na mirmishi kuma yana jinjina kai,Bai katseshi ba sai da ya gama kafin yace"Saleem..." ya kirasa da muryansa cikin taushi da kulawa dagowa yayi yana kallonsa Kai Daddy ya kada mai yana Fadin"Taso kazo kusa dani kaji..."Bai yi gaddama ba,yaja jiki zuwa kusa Da daddy,wanda ya kama duka hannuwanshi ya rike gam,yana kallonsa ido cikin ido kafin yace"Bantana rike ka araina ba Saleem,saima Dadin Abunda ka aikata Naji,ko banza kafara Daidaita rayuwar malika,ni kuma kasa na gane gaskiyan dana gaza ganewa shekara da shekara,Hakika zuwanka Rayuwar Malika Saleem haske ne,kuma Rahama ne,dama aikinka ne kai kafara kuma kai zaka karisa,Malika zata bika,duk inda zaka sanya kafa zata saka Domin na bar duka amanarta ahannunka ne Saleem..."Ya fada kwallah tana cikamai ido ... Gabadaya gwiwan Saleem tayi sanyi yama kasa mgana,ya bude baki zaiyi mgana kenan hajiya binta ta dawo dakin tana tambayan Saleem ko akawo mai lunch ne,girgiza mata kai yayi batare da yayi mgana ba,Daddy ne ya kalleta yana Fadin"Binta taimakeni ki kiramun Bby,ki kuma umarci yan aikinta da su hadamata duka Abunda zata bukata acikin akwatunata,,ga mijinta nan zai wuce da ita yanzu..."Yafada daidai sanda kwallar dayake rikewa ta zubomai,Hajiya binta bata ce komai ba ta juya tafita,Shiko saleem yana ganin sanda hawayen Daddy ke diga bisa hannunshi,ammh yakasa kwakwaran motsi saboda kalmar nan da Daddy ya Furta na yabashi duka *AMANARTA*..." Hajiya Binta zaune ta iske Malika tana cin abinci tashinta daga barci kenan,sakon Daddynta ta sanar da ita,bata bar dakin ba har sai da malika ta mike sanye da doguwar riga baka na kamfanin Armani,wanda bakin Siririn gyalen dake kanta ta sakaloshi zuwa wuyanta,kallo daya zakamata ka Fahimci tana da shigar karamin ciki,kodon ganin yadda tayi wani danya sharaf da ita,sai da ta Fice zuwa Falon na Daddy kafin Hajiya Binta ta Umarci su Dose da su hadama Malika duka kayanta na anfani cikin manyan akwatunanta,amsa mata sukayi da toh kafin su Shiga ciki su fara hada mata kayan. Bata da masaniyar zuwan saleem,domin Tun safe tana daki bata Fito ba,shiyasa kanta tsaye ta shiga falon ko sallama batayi ba,don ba halin malika bane shiga waje da sallama,Bata lurama da Saleem dake durkushe gaban Daddy ba,wanda duka hannuwanshi ke hannu Daddyn kamar mai rokon wani Abu. Tana zuwa ta duka ta bashi peck agoshi tana Fadin"Dadylove ya jikin ka..? Hajiya tace kana kirana hop dai ba wata damuwa ko..? Tafada tana kokarin dukawa kusa dashi,sai ji tayi cinyarta ya gogi Gwiwan kafar wani azabure ta kalli inda taji Abun yatabata,shima daidai lokacin ya dago suka ko Hada Four eyes dashi. Dam!Dam!Dam! gaban malika ya buga bayan ya amsa lokaci daya,ko mutuwa tayi ta dawo bazata taba mantawa da wannan muguwar Fuskar ba,wacce bata cike da komai sai mugunta da zalunci uwa uba rashin imani,Ai sai ga Malika saboda tsoro da razana tayi baya zata Fadi Allah ya taimaketa ta rike karfen keken Daddy,ta zauni da duwawunta dabas akasa,ko"ina na jikinta babu inda baya rawa kafin kace me ta kamkame jikinta hawaye ya Shiga wanke mata fuska,Shiko saleem kallo daya yayi mata bai kara,don in ya cigaba da kallon Fuskar shegiya zai iya tashi ya zubamata marunka da zatayi hawaye mai dalili gaban Ubanta,kauda kai yayi yana jan Allah isa Aransa,sai daga bayama yake Tunanin me ma yasa ya dawo kasar? kai gaskiya Abbi bai mai Adalci ba. Daddy daya lura da yanayin malika Sai ya saki hannun Saleem guda daya ya mika mata yana Fadin"Taho Babby,mijinki ne yazo tafiya dake..."wani yam! taji lokaci daya kanta ya sara da karfi Dafe kirji Tayi kafin tace"No Daddy.....No...",Take Fada tana sharan kwallah gwanin ban tsausayi Girgiza mata kai yayi kafin yace"A"a Babby karki ce haka,plz come closer kinji..."Yake Fada yana mikamata hannu,shiko saleem aransa addu"a yake Allah yasa kartace zata bishi,ammh sai addu"arsa bata karbu ba,jikinta na rawa ta matso ga Daddy kafin ta damkamishi hannunta kwara daya hada hannunta yayi dana Saleem waje daya ya damke,dukkansu sai da sukaji wani Shock yajasu,tare dukkansu suka saki ajiyar zuciya suna Runtse ido. Daddy ya kalli Saleem yana Fadin"Saleem ga Malika nan,Na damka amanarta da amanar rayuwarta a hannunka na har abada,kai ne, uwarta kai ne ubanta yanzu,Saleem ina da kyakyawan Shaida akanka,don Allah kada ka bani kunya kayimin alfarman tsayawa tsayin daka wajen kula da tarbiyan Malika,ka koyar da ita ko kadan ne daga cikin Abunda ka sani,kazamo wa gareta,ka zamo mata kani,bayan kazama mata shafin wani kawa ko aboki, Don Allah don darajar iyayenka kada kabar rayuwar Malika ta sake lalacewa akaro na biyu,bata da wani gata anan Duniya yanzu sai kai,ni yanzu tawa ta kare,ba lalle bane na sake daura wasu shekarun araye ..."Ya fada kuka ya kwace mai,Wani kuka ne yazoma ma Malika da karfin gaske ta fada jikin Daddy tana saka kanta bisa cinyarsa tana gunjin kuka take Fadin "plz Daddy Don't let me go..."plz...."Take Fada tana kuka mai cinrai,hannayensu ya saki kafin ya kama kan,Malika yana tashafawa alamar lallashi muryansa cikin karaya yake Fadin"Am srry Babby kidaina kuka kinji ko,ko bani na tabbata saleem,da mahaifansa baza su barki kiyi kukan maraici ba,Ki bishi sau da kafa,kiyimai biyayyah,ki kuma guji Abunda bayaso,Don Allah Malika kibi mijinki Duk Abunda yace kiyi kiyishi matukar bai sabama shari"a ba kinji ko.."Gyada mai kai takeyi tana kuka kamar zata Shide shima hawayen yake. Saleem dake gefe shima kamar yayima Daddy kwallah,saboda yadda suka bashi tsausayi,baisan sadda yasaka Tattausan hannunshi yana Sharema Daddy kwallah ba kafin ya koma ya dago Malika yana kallon cikin idanuwanta cike da wani yanayi wanda Shikadai ya barma kansa,sani itako,runtse idanuwanta tayi tana jin wani Fargaba acikin zuciyarta Hannaunta ya damka ya damke da karfi yana Fadin"Na karbi Amanarka Daddy da zuciya daya kuma nayi maka alqawarin ni Saleem kabir kumo zan kula da Malika Fiye da yadda zan kula da kaina,zan tarbiyarta da ita kamar yadda uwa zata tarbiyarta da yarta,zan bata kulawa tamkar yadda yaya zai kula da kanwarsa,Sai dai Abunda na gaza zan barma Allah sauran.."Ya fada yana hada duka hannunsu su uku ya damke atare. Daddy na hawayen Farinciki yana ma Saleem godiya kafin ya kalli Malika yana Fadin"Ki tashi kije ki Shirya babby,daganan ki tahomin da mukallayen gidan nan dana motocin nan,tare da takardan sakamakon likita game da cikin da kike dauke dashi..."Dam!Gaban saleem ya buga,da rawan baki ya kalli Daddy yana Fadin",Ci..ki....Ma...Li....Ka.....Ke...Da...Shi...."? Yafada bakinsa na rawa,gyada mai kai Daddy yayi yana Dafa kanshi daidai lokacin da Malika ta mike tana shesshekan kuka ta Fice,Wani yanayi Saleem yaji sai ya samu kanshi da kurama bayan Malika ido,yana Jin wani iri acikin ranshi,ciki kuma? kai yanzu wai har ya isa yin ma mace ciki...? Bai gama mamaki ba,yaji Daddy na gayamai jikin da malika takeji,gyada mai kai kawai yakeyi yana kiyasta abubuwa da dama cikin ransa,gefe na zuciyarsa na Farinciki ammh kuma wani shashe na fadin"Koda cikin sai ta ci ubanta,ai babu daga kafa yarinya..." Ba Malika takawo makullyan ba,Hajiya binta ta kawo,shiko Daddy ya hada duka ya damkama Saleem yana Fadin"Duka kyautar danayi maka,da zuciya daya nayi maka shi,saboda haka gasunan na maida maka,sai dai in bakaso ka kyautar dasu,duka mallakinka ne.."Girgiza kai yayi yana bin takardan sakamakon Cikin Malika yana Fadin"Bazan kyautar ba Daddy,ko wanchan karan dana dawo dashi rashin sani ne,ammh wannan karan na karba kyautan naka da hannu bibbiyu Allah ya saka da alheri ya kuma baka lafiya.."Da Ameen ya amsa yana ta sakamai albarka. Malika ko tana chan tana ta kuka kamar za"a zareta ma rai,Hajiya binta ke ta lallashinta,bata chanza kaya ba da wannan bakar dogowar rigar hajiya ta riko hannunta suka nufo dakin Daddy,yayinda da Su Dose suka fara Fita da manyan akwatunanta guda uku suma jikinsu duk yayi sanyi na Tafiyar madam dinsu,wanda suna zaton wannan karon bada su za"a tafi ba. Gaban Daday da saleem ta durkusar da ita tana Fadin"An gama hada komai,sun Fita da kayan zuwa waje..."Saleem najin haka ya mike yana duba agogon hannunshi,biyu saura na rana,Kallon Daddy yayi yana Fadin"Toh shikenan Daddy mu zamu Wuce kada muyi dare bisa hanya.."Kallonsa Daddy yayi yana Fadin"Haba Saleem kamar na koranku kubari kuci abinci kuyi sallah sai ku dau hanya ko.."Saurin cewa yayi "No Daddy karka damu zamu tsaya bisa hanya muci abinci muyi sallah,bani so muyi dare ne..." Shuru Daddy yayi kafin yace"Shikenann Saleem Allah ya kiyaye hanya,ngd sosai ka gaida su Kumo din Allah ya kaddara saduwa..."Da Ameen ya amsa yana mikamai hannu suka sake musabaha kafin yafara taku zai Fice daga Falon,da hanzari Daddy yafara tura kekenshi zuwa cikin bedroom dinsa yana fadin cikin wata irin murya.."Binta ki Fita da Malika daga dakin nan,bani son ganin tafiyarta don Allah..."Yafada yana tsiyayan hawaye,Jin haka yasa malikar kwace jikinta dagana Hajiya binta ta bishi da gudu ta rumgume bayanshi tana Fadib"Wayyo Allah!Daddy na....."Take Fada tana kuka kamar zata shide,bai saurareta ba,yana share kwallah,ya cigaba da tura keken zuwa cikin bedroom dinshi yana Fadin"Kije Babby,insha Allahu nan gaba zaki zama Abun alfaharin ya"yanki da al"ummah baki daya koda bana raye,kije Allah yayimiki Albarka yakuma zaunar dake lafiya agidan mijinki..."Yafada yana wani kuka na zuwarma,tura kofar bedroom din nasa yayi ya shige yana Rufe kofar.... Zuciyarsa ke bugawa da karfi tana Fat!Fat!Ammh kuma gefe daya Farinciki yake na ganin ya sauke wannan Nauyin dake kanshi wanda ke damunshi Shekara da shekaru,na damka amanar Malika hannun wanda zai gyara mata rayuwarta daga Duhu zuwa haske,kuka yake yana Fadin"Allah na tuba Allah ka yafemin ya Allah..Astagafurrillah.!"Yake Fada yana daga hannunshi sama hawaye suna zuraromai..! _Wayyo Allah!wlh Sai  da nayi kuka😭Wannan page din ina rubutashi inaji yana tabamun zuciya sosai...Kai Allah kadamu da kyakyawan kaddara,ka kuma bani damar yin Nadama cikin lokacin irin na Daddy,ba sai lokaci ya kuremana ba kamar Fir'Auna..,Allah ka tsaremu Ameen_ Nan wajen Malika ta Fadi tana gunjin kuka,Hajiya binta ne ta kamata tana lallashinta ita ta rikota har suka sauko Falon kasa inda Su Atika da Dose suke tsaye suna share kwallah tsausayin Madam dinsu da kewarta,Kallonsu takeyi sai taji yau sune fa yan"uwanta don dasu ta saba,tayi musu tsawa,tayi musu Fada,ta wulakantasu,ta dakesu,ammh sai gashi yau suna kuka don zata rabu dasu,ashe ba Farinciki zasu yi ba,don zasu rabu da ita ba..? batasan sadda tatafi da gudu ba ta fada jikinsu tana kuka ba,Suma kamata sukayi suka Rugume suna Fadin,"Plz madam we are going wit u" Girgiza musu kai takeyi kafin ta dago tana share musu kwallah dukkansu kafin tace"No,stay here...buh i promise u zan zo na tafi daku insha Allahu kunji,stop craying Sweetheart ,and tanque very much For u Time,May god bless u Ameen..."Wani kuka ne ya kwace mata tayi baya da Sauri tana daga musu hannu. Gaban Hajiya taje ta durkusa tana Fadin"kiyafemin *MOMMY*..."Take Fada kanta sunkuye tana kuka,Wani tsausayi da sanyi ya kama Hajiya ta duka ta dagota tana Share mata kwallah tana Fadin"Bakomai yata,dama banta ba rike ki ba,Kisani tamkar yata joda haka na daukeki,shawarata gareki Shine  kibi dukkan Abunda Mijinki ya umarceki,komai kike bukata ga iyayen mijinki nan,ki tambayesu komai kike bukata zasu baki shi, Abu na karshe ga waya nan,zamu dinga kiranki muna tambayanki lafiyanki,daga karshe don Allah malika ki kula da kanki da kuma cikin dake jikin yanzu dai baki da kowa sai Allah sai mijinki kinji ko? . Fadawa jikinta kawai Malika tayi tana kuka take Fadin"Naji Mommy,kuma insha Allahu zanyi amfani da shawaranki Nagode sosai.."Take Fada tana share kwallah,Megadi ne ya shigo yana sanar dasu Yallabai yace Madam ta Fito su Tafi,jikinta ba kwari ta daga kafa ta fara tafiya tana karama Falonsu kallon Sai watarana,ahaka har ta Fice bata waigo ba itama hajiyar sai taji kwallar na silalo mata,Su Dose ko faduwa sukayi suka kamkame juna ita da merry suna kukan tsusayama madam dinsu,don daga ganin fuskar mijin nata baida imani,balle sun tsorata dashi Tun kusa kashe musu madam dinsu da yayi. Cikin kukan ta Fito tanayi tana sharbe kwallah,nan ta iske joy da peter tsaye suna zare ido,kallonsu kawai tayi sai tasamu kanta dayi musu mirmishi tana daga musu hannu,saleem na tsaye jingine jikin motarsa yana kallonta wani wawan tsaki yaja kafin ya kauda kai,jikinta asanyaye ta kariso gabanshi tana rawan jiki,kallon sama da kasa yayi mata kafin ya bude baki yace. "Ke..."Afirgice ta dago idanuwanta da sukayi jawur saboda kuka tana kallonshi Ware mata ido yayi yana Fadin"Uban wa zaki bi da wannan dan Figigin mayafin...? Yafada yana jefamata wani banzan kallo,baya taja tana saka hannu tana goge kwallar da suka zubomata takasa cewa komai,ganin ta maidashi wani mahaukaci ne yasa ya daka mata tsawa yana Fadin"Ke bada ke nake mgana ba,dont force me to mention my First statement,wlh bazaki ji da dadi ba.." Yafada yana kada mata yatsunsa,Bakinta na rawa Tace"Ba..ni...da..wa...Ni...."Harara ya sakarmata yana Fadin"Au baki da wani ko? kodayake banyi mamaki ba,saboda ba addinin aka sani ba,comon jare,ki koma ki sako hijabi ko na waye kizo mu tafi in ba haka ba,i swear bazaki shigarmin mota da wannan Shigar ba,ba dan iska bane ni..."ya fada yana zagayawa bangare Direba da hanzari. Batayi gadddama ba,da hanzari ta koma cikin gida.bata ga kowa afalon ba,dakin hajiya kawai ta shiga ta bude wardrope dinta taci karo da wani Farin hijabinta,dauka kawai tayi ta saka tana Ficewa daga dakin Da hajiya sukaci karo,wacce ta kalli malika da mamaki kafin tayi mgana Malikar ta rigata da cewa"Yi hakuri mommy na Ari hijabinki ne.."Tafada tana mata mirmishin yake. Baki Hajiya ta washe tana fadin",Masha Allah...Maza Allah ya kiyaye hanya kai madallah da samun Surikiin kwarai yau Malikar Daddy ce harda Hijabi..? Tafada tana Mata dariya,mirmishi kawai tayi kafin ta juya Ta fice,hajiya ta bita da kallon mamaki tana mai jin dadi sosai na gamin yadda komai zai tafi kan lokaci Hajabin yadi uku ne,itama hajiyar Joda ta dinkamawa,so bai kai mata kasa ba,ammh tayi kyau sosai kamar ba malika ba,don yau itace rana ta farko data taba saka hijabi haka,Tun daga nesa yake hangota sakin baki yayi yana kallonta aransa yana Fadin So cute ashema hijabin yafi mata kyau,tana kariso ya riga daya bude mata gaban motan,shiga kawai tayi,shikuma yana kokarin tada mota dama alreday ya daura Set belt,tana jinsa yana karanta addu"ar matafiya kafin ya tada mota,suyi kwana, hon ya zubama megadi da hanzari ya wangale musu get suka sulala waje su peter na daga musu hannu. _Ammh ta hanyar nuna min kauna da soyayyarku wajen Siyan *MALIKA MALIK* Akan Naira 200 kachal👌,ta wannan account Nombar, *0552179550 JAMILA UMAR GTB,sai ki Turo Shaidan biya ta wannan nombar *09069067488* ko kuma katin waya na MTN,shima sai ki Dauki hoton katin aturo kai tsaye ta wannan Nombar *09069067488* Sai kun zo ina maraba daku masoyana.._ *Karku manta da garabasanmu mai son Siyan Biyu KISHIN MATA,na HAFNAN,300 ne kachal👌shima zai iya Turo ta nombar bankin dana bada ko katin waya na MTN ta nombar saman dana bada, ko kuma kai tsaye ku Tuntubemu ta wadannan Nombobin domin karin bayani*... 07065481260..Ko kuma 09069067488 Shakira. *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *KURIKE GIRMAN AMANAR DANA BAKU,KUYI MIN ADALCI KAMAR YADDA NAYI MUKU KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*👏 *15* ..........................."Tunda Suka dau hanya bai kara koda kallon inda take ba,Tukinshi kawai yake,sai da sukayi nisa kana ya Saka karatun alqur'ani cikin kira"ar Mallam Abdullahi Abba,cikin Suratul Maryam,cikin kwarewa da zakin murya da hadda mai dorewa yake bin karatun..... Tun tana rakube gefe,tana kallonsa Abun na burgeta hardai ta saki jikinta tana morema kallonshi,sai taga kamar zai waigo,sai tayi saurin kauda kai tana Kalle kalle,shiko yana ankare da ita,kawai ya barsane saboda baisan yawan mgana kada yarinya ta rainashi,duk da mawuyacin abune hakan tafaru,duba da yarda ya darsar da Tsoro mai girma azuciyarta. Tuntana jin dadin Tafiyar har ya Fita kanta,don wannan Shine karo na Farko datayi tafiyan mota mai tsawo haka,Tun tana kalle kallen hanya,har dai wani Barci mai dadi da Nauyi ya kwasheta,bata farka ba sai dataji yana daka mata tsawa da Fadin "Ke..."Firgita tayi tatashi da hanzari tana mutseke idonta daya chanza kala,saboda barci,tsaki yaja ya bude murfin motan ya Fita,sai lokacin ta waiga taga motar su ta tsaya abakin wani masallaci haka,agabansu taga wani Symbol an Rubuta *WELCOME TO ZARIA..* Gyara zama Tayi tana bin wajen da kallo yadda yake da Hada hadar mutane,ga masu saide saide,nan kowa nata sha"aninsa waje kamar kasuwa,tabe baki tayi tana ganinshi ya tsallaka titi yaje ya dauki buta ya zuba Ruwa yashige wani lungu,da alamu zai kama Ruwa ne,sai zuwa chan taga ya Fito yaduka yafara alwala,har ya idar tana kallonshi ta kuramai ido ta cikin mota,tana mamakin yadda taga shi alwalanshi dabam dana mutane😂kodai naki ne daban Hajja malika. Agaban idonta ya Shiga masallacin ya dau tsawon mintina kafin ya Fito,kai tsaye ya tsallako Titin yazo ya bude mota ya shiga itako Tun lokacin data hangi wani mai doya da kwai yana soyawa taji miyanta ya tsinke taji shi take bukatar ci,har ya tada motar tana ta kallon Doya da kwan,inda take kallo ya kallah kafin yace"Ke lafiyanki kuwa kika kurama bawan Allah ido yana kan sana"arshi.."? Hadiye miyau tayi tana kyafta ido,kamar wacce tayi karya,Sake baki yayi yana kallonta yadda takara kafe mai doya da kwai da ido,Girgiza kai yayi yana Fadin"Wai miye haka? ko zaki ci ne..? Da sauri ta gyada mai kai tana kara kallon mai doya da kwan,Sake baki yayi yana kallonta kur kafin yace"Ke kina da hankali kuwa? wanchan doyan da ya wuni awajen tun safe all Diseases sun gama sauka akanshi..? Sadda kai tayi tana Share kwallah kamar wata yarinya bai yi mgana ba,illa balle murfin mota dayayi ya Fice da kanshi ya tsallaka wajen mai Doya da kwan ya Siyomata na 1k cikin leda,ya kawo mata,jikinta na rawa ta cafki ledan ta bude har miyanta nabuzowa ta Shiga ci hannu baka hannu kwarya. Hannu ya harde kawai akirji yana kallonta yadda take tusa doyan kamar ta samu abinci,aransa yana mamakin kodai yunwa takeji ne? bai samu zarafin mgana ba,saboda ganin ta kusa cinye doya da kwan,haba ya rike kawai yana kallonta cike da mamaki,Haushin kanshi ma yaji da kallonta dayakeyi tsaki yaja ciki ciki ya Kunna motar yatadata suka Fara tafiya cikin slow. Itako Malika hankalinta kwance take cin Abunta,sai dai kuma chan sai zuciyarta tafara tashi,dakatawa tayi tana yamutsa Fuska,ta ture ledan tana toshe bakinta sboda yunkurin Amai data Fara,Kallonta yayi rabin hankalinsa naga driving Yana Fadin"Ke wai lafiyan ki kuwa..? Hannunta na bakinta tace"Amai nakeji.."Tsaki yaja da karfi yana kokarin samun wajen parking yake Fadin"Ba dole kiji amai ba,kalli fa Abunda kika yabama cikinki,kina ci kuma babu Natsuwa..."Yafada daidai yana parking din motar,kogama tsayawa batayi ba ta balle murfin motan ta Fice da gudu,nan bakin Titin ta gudu ta Shiga kelaya amai gwanin ban tsausayi,Fitowa yayi yana kallonta cike da takaichi yadda ta tara mai jama"a marasa gani su kyale,wani ma cewa yayi haba yallabai kamata mana wai sannu baiwar Allah"Haushin hakane yasa yaki karisawa gareta,sai dai kuma karfinta ya kare,don duk Abunda ke cikinta sai da ya Fito,tun tana yunkurin Aman harta kai tana neman Faduwa daga durkushewan. Cikin Zafin Nama ya isa gareta ya Rikota da hanzari yana Fadin"Ke miye haka..? luuu tatafi jikinsa tana neman gadashi,Rikon ya tsaurara yana binta da kallo yadda ta bata gaban Hijabinta da amai da kuma bakinta,Saboda yadda jikinta yayi lakws ko idanuwanta bata iya budewa,Rasa yadda zai yi da ita yayi kawai sai ya zaunar da ita da karfi akasa yana Fadin"Ki zauna Dakyau zani mota na dauko miki Ruwane,in kuma kika saki jiki wlh kisha kasa no my water inside.."Ya fada yana Sakinta da hanzarin ta Daba duka hannyenta akasa ta dafe kada tasha kasa don ta lura Saleem kan babu mutumci A al"amarinsa. Cikin motan ya koma ya dauko mata ruwan goranshi,tun da sh ma'aboci shan Ruwa ne,baya rasashi yana zuwa ya bude ya mika mata,jikinta na rawa ta karba sai dai kuma ruwan na neman barewa saboda Bata da karfi jiki,saurin rikewa yayi yana zabgamata harara bai Saurareta ba ya shiga kwararamata Ruwan agaban Hijabinta aman ya Gangara,ammh bai saka hannunshi ba,hannunta yace ta tara ya zuba mata Ruwa,Ta kuskure bakinta ta zubar sau uku kafin ya zubamata ta wanke Fuska,yana shirin zubda Sauran Ruwan ne tace ahankali.."Zan sha ruwa..."Bai kalleta ya mikamata kawai aransa yana jin Haushin kansa,kawai an cuceshi an hanashi kuka. Sai da tasha ruwan sosai kafin ta zubda Sauran Tana ajiyar Zuciya Kallonta yayi yana duba agogon Fatan dake hannunsa yana Fadin"Kinga Malama zaki tashi mu tafi ne,ko kuwa ni nayi gaba ne..? yafada yana Wani kallonta a hagunce,Tana jin haka tafara kokarin mikewa,ammh kuma takasa,saboda kanta dataji yayimata Nauyi,dafe kasa tayi tana cije baki ta samu ta mike tana Mustsike ido,ammh kuma kafafunta na rawa,ganin zatayi baya yasa tayi hanzarin mikamai hannu ya kamata,ada yaso yaki mikamata hannun nashi ne,ammh ganin dayayi zata Fadi da gasken shiyasa ya mika mata hannunsa da karfi ya rikota tayo Rimi ta fado jikinsa bata samu masauki ako"ina ba sai Afaffadan kirjinsa. Dukkansu sai da jikinsu ya amsa,shi harda sakin ajiyar zuciya ammh Siririya,ganin suna bisa Titi ne,kuma mutane na Wucewa suna ganinsu,shiyasa ya sassauta rikon dayayi mata yana Fadin"Ke miye haka,baki da kunya ko? yafada yana kallonta cikon ido,bata kulashi ba Tunda ta samu ta iya tsayuwa da kafarta sai kawai ta sakeshi ta Wuce ta Shiga mota tana sauke Numfashi. Tabe baki yayi Ya shige bangaren Direba yana kokarin tashin motan ne yaji muryanta tana Fadin"Ban yi sallah ba.."Bai ko kalleta ba sai da ya tashi motan ya daidaita bisa Kwalta kafin ya kalleta yana Fadin"Ke wai don Allah hala ni bawanki ne? karki ka ga nayi Shuru na kyaleki kina Abunda kika dama,Tun dazu daga kice wannan sai kice wannan,kamar kin samu wani sakarai ko bawa,Toh bari kiji kada ki dauka don Mahaifinki yabani amanarki,zan lalace agindi ina miki bauta ba,u bettee stand up yarinya,don Wlh ni ba bawanki bane,uselless girl kawai..."Yafada yana Huci. Hawaye suka wanke mata Fuska ta sadda kai tana Sharbewa wani wawan tsaki yaja yana Fadin"Ji bakinta don Allah,wai banyi sallah ba..? Ke dama kina sallah ne,kin ma san wani Abu waishi addini ,tsayama don Allah plz ke musulma ce..? Yafada yana kallonta kai tsaye duka hannunsa na kan Sitiyari yana murzawa,dagowa tayi ta kallesa Idanuwanta cike da mamaki bata samu zarafin mgna ba ya katseta da cewa"Eh nace ke Musulma ce? Koda ke musulma ce,ina tamtama da addininki don ban yarda da Kalmar shahadanki ba,sai na kara fada miki kin tabbatarmin tukunnah.." Jagale Tayi tana kallonsa cike da mamaki,gefe daya kuma Zuciyarta cike da tsoro na,hallayar Saleem wadanda suke Fitowa daki daki,ganin yadda take kallonsa tana tsiyayan hawaye yasa ya watsamata harara yana Fadin"Stop looking at me,in ba haka ba yanzu na chanza ma Fuskarki kammani,Bush girl.." Tana jin haka ta maida kanta gefe,tana tsiyayan hawaye,kukan tsausayin kanta na kamata,tanayi tana saka gefen hijabinta tana Sharewa hawaye dagan motar ta dau Shuru,tuni ya taka motar yana Gudu son Ranshi kamar zai tashi sama.Itako Tun tana kuka har ta hakura wani barci ya sake kwasheta ta sulale bisa kujeran motan tana barcinta,sau daya ya kalleta bai kara,ammh Ransa in yayi dubu ya baci gabadaya an kashemai Rayuwa,tsakani ga Allah. Yana shiga gidansu Ana kira kiran sallah mangariba,har yasa motar nashi aparking space Malika bata Farka ba,shikuma bai tasheta ba,sai da ya Fito ya bude booth din motar Megadi ya cida akwatunanta zuwa cikin gida yana masa barka da zuwa,Bude motar yayi inda take ya duka ya fara marin kumatunta yana Fadin"Ke..Ke..Tashi mana.."Dakyar Ta bude ido tana binshi da kallo idanuwanta suna budewa dakyar. Gaba yayi yana kokarin ciro wayarsa Daga aljihu wacce ke neman Dauki,sunan Abbi yagani,bai daga ba illah waigowa da yayi yana kallonta ta Fito daga motar tana tafiya dakyar,Wani kallo yake mata na lalle yarinyarnan,ganinshi tsaye yana jiranta yasa ta daga kafa ta cimmai,bai mata mgana ba,yayi gaba tana binshi abaya tana kallonsa yadda yake komai cikin izza da jarumta,Aranta tana Fadin ga Namiji har Namiji ammh ya bata kanshi da mugunta da mugun Hali.    Ummi na zaune Afalo ita da Hajiya suna hira,suka ga megadi na Shigo da akwatuna,cike da mamaki suke binsa da kallo har ya dire Akwatun a tsakiyar Falon yana haki,Hajiya tace"Kai daga ina kuma wadanan kayan? Bakinsa awashe yake Fadin"Magajin yallabai ne,ya iso yanzu.."Kowa yasan haka yake cemai Basu samu zarafin mgana ba,sukaji sallamar Saleem ya Shigo Falon bayanshi kuma Malika ce tana Tafe tana kalle kalle. Da hanzari Ummi da hajiya suka mike,Hajiya ce ke Fadin"Lale..Lale marhababiki.."Take Fada bakinta washe,lokaci daya da"a tarihin rayuwar malika datataba dukawa tana gaida wani,har kasa ta zube saman cafet tana Fadin"Ina yini.."Bakinta na rawa,Hawaye na tarowa a idanuwanta,tarota hajiya tayi tana Fadin"A'a tashi ya'nan nan ma ai gidanku ne.."Saleem dake gefe yaji kamar ya make Hajiya saboda shisshiginta,Tsaki yaja aciki yana kallon Ummi yace"Ummi na Fita yanzu ko? Hararansa tayi tana Fadin"Bansani ba..."Kwabe Fuska yayi kamar zaiyi kuka yake Fadin"Nidai wlh An tsaneni agidan nan,daga dawowata ba wanda yayi kewata,Abbi ya koroni ke kuma yanzu kina hararata.." Malika dake zaune kan kujera kusa da Hajiya take binshi da kallon mamaki,ashe dama ya iya mgana cikin Dadin rai,Bata gama mamaki ba taga Ummi taja kunni da karfi kafin ta Mangareshi a keya tana Fadin"Eh din an tsaneka ka gyara halinka in kaji haushi.."Kara yasa yana yarfe hannu yana kuma rike kunnashi Dariya hajiya tayi tana Fadin"Ke Aisha,wannan ai ba duka bane tabashi kikeyi,ki gaframai mari mai zafi kigani in zai kara mgana.." Wani bad look yabama Hajiya kafin ya Daga hannu yana Fadin"Eh sannu fa,toh bata gafrin ba ko ke zaki Gafra min ne,Uwata..."Mikewa tayi tana Fadin"Sosaima kuwa yaro.."Ganin Ta nufoshi gadan gadan yasa ya arce da gudu,sai suka ci karo da Abbi wanda saukowanshi kenan jin hayaniya,Rikesa yayi yana bin Ummi da kallo wacce ke gefen malika suna gaisawa,Yana ganin Abbi sai ya kame hannunshi A gefen kunnenshi yana Fadin. "Sir..."Mirmishi yayi mai kafin shima kawai ya kamemai,dariya su Ummi suka saka ita da Hajiya itako Malika mamaki Saleem ke bata,ashe ya iya mu"amala da mutane haka? Rikosa Abbi yayi har zuwa wajen dasu Malika suke,wanda tayi saurin mikewa tana gaishesa da Abbi,saboda kunya mutumin ba tun yau ba,tun yana zuwa duba Daddynta. Amsa mata yayi yana tambayanta ya Daddnyta da jiki asanyaye take karbamai,Ummi ya kallah yana Fadin"Kamata Aisha ki rakata dakin Saleem din,ki saki jikin yata,nan ma kamar gidan ku ne kinji..? Gyada kai tayi,ammh gefe na zuciyarta na rawa da Fargaba hade da tsoro,na jin ance a kaita dakin Saleem. Shima yana jin haka ya gimtse Fuska yana Fadin"Dakina kuma Abbi? ina laifin Saleema,tunda yar'uwantace mace.."Karo na Farko Da Daddy ya mangareshi akai yana Fadin"kaga naka nan, don yar"uwantace mace,ko saleeman na nan ai kafita kusanci da ita,ba matarka bace ok baka tuba ba ko,dama tuban na karya ne.."?Da sauri ya rike hannun Abbi yana Fadin"No Abbi wlh Tuban gaskiya ne,nakuma yi niyyah bazan kara aikata makamancin haka ba.."Gyada mai kai yayi yana Fadin"Gud..Maza dauki kayanta ka shigar mata dashi,ke kuma Ummin Marwan,ki sama mata Abunda zataci Tunda sunsha tafiya..." Hajiya tace"Gaskiya kam,gashi kuma kusan mace mai shigan karamin ciki yanzu duk jikinta yayi mata Nauyi. "Afakaice ya zabgama Hajiya harara yana kunkuni aranshi,yana gani Ummi ta rike malika suka nufi dakinshi kamar ya kurma ihu ba dama. Kan daya daga cikin Kujerun Falon Abbi ya zauna yana Fadin"Yanzu mukayi waya da Alhaji Abdulmalik yana tambayana ko kun kariso nace haryanzu baku zo ba,yace yana ta kiran wayoyinku duka bai samu ba,kakirasa ka shaidamai kun iso.."Da Tom ya amsa yana latsa wayarsa bai sanar da Abbi tun wanchan lokacin ya sagale Nombar Daddy ba,sai ya lallaba ya ciresa daga blacklist,kafin ya kirasa Yadaga suka gaisa kafin ya sanar dashi sun iso,gama Abbi zai mai mgana,cike da fara"a Abbi ya karba suka gaisa kafin su cigaba da tattaunawa,daga karshe Abbi ya tabbatarmai da cewa kada ya damu insha Allahu zai kula da rayuwar malika tamkar yadda zai kula da Da'nsa Saleem,Daddy yaji dadin haka sosai,sukayi sallama cike da Farinciki. Mikamsa wayarsa Abbi yayi yana Fadin"Dauki kayanta ka shiga mata dashi ciki.."Jiki asanyaye ya mike aransa yana Fadin"Karyata takusa karewa,daga ramuwa na koma dan dakon kaya..."Yake fada yana daukan manyan akwatun guda biyu ya nufi dakinshi yana Ayyana yadda zai Fita daga wannan gadar zaren daya Fada. Yana Shiga dakin nasa,ya tarar da Ummi zaune gefen gadonshi ita da Malika,da alama mgana take mata,ita kuma malika tana gyada kai,wani haushi ya kamashi kai tsaye ya wuce wajen makeken wardrope dinshi yana ijiye akwatunan,ya juya zai Fita kenan Ummi ta mike tana Fadin"ina zaka,dawo ka hadamata ruwan wanka,tayi sallah,ni kuma bari naje na hado muku Abincinku ko.." bai waigo ba yaji ya daskare atsaye saboda wani kololin Abu dayazomai Wuya,Ummi bata Fahimci halin dayake ciki ba ta Fice tana jawo musu kofa,Juyowa yayi yana kallon Malika wacce kanta ke duke tana wasa da zabban hannunta. Kugunshi ya kama da hannu Biyu yana Fadin"Kuturin bala"i kenan ruwan wanka?lalle ya kamata nazo nayi gaba Tunkafin na tashi daga *SAI NA RAMA* na koma _SALEEM BAWAN MALIKA_………" Yafada yana jin Tukukin Abun har cikin ransa,Itako tana zaune,sai da mganar ta kusa sata dariya,tayi saurin Rufe baki tana rawan jiki,Ganin ya Tsuramata ido yana kallonta cikin ni ki kema dariya? lalle zaki ci ubanki yanzu kuwa.." Bai kara kallonta ba,ya shige tailet din da karfi ya bango kofar kamar zai ballah,ajiyar zuciya ta sauke kafin ta fara bin dakin da kallo,komai neat,kamar ba dakin Namiji ba,koda yake ta lura mugun baida kazanta yanaji da kansa. Am srry wlh yau din sai aslow,ku karanta da hakuri... Janaf. *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *KURIKE GIRMAN AMANAR DANA BAKU,KUYI MIN ADALCI KAMAR YADDA NAYI MUKU KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*👏 *16*       Tun tana saran Fitowarshi har taga bashi da niyyar Fitowa,sai chan sai gashi ya Fito,sanye da wani Towel mai dan girma,hannunsa kuma yana saman kanshi dauke da wani karamin Towel din yana goge ruwan dake kanshi Kallo Daya tayimai tayi Saurin Sadda kanta kasa,saboda yadda ya Fito gabadaya kirjinsa dake lullube da gargasa,awaje yana maiko Ruwa yana bayyane,Suffar karfin hannayensa ma"ana muscles suma sun bayyana waje,shima ko barayinta bai kalla ba,balle ya tankata ko yasan akwai tsayuwar mutum awajen. Wajen Dressing morrior dinsa ya nufa,yafara Shafe jikinsa da lotsin dinsa mai dadin kamshi,har yagama yayi cumbing din sumar kanshi bata ko kara motsi daga wajen ba,Wucewa yazo yi ta gabanta zai isa wajen wardrope dinsa,kafarta dake wajen ya bangaza kamar bai gani  ba,nan ko da gangan na haushi ya hadamata Ruwan wanka ne. Jaye kafarta tayi tana Kwabe Fuska saboda taji zafi ko kallonta bai yi ba,yakarisa wajen wardrope dinshi ya bude yana dauko kayan da zai saka,wasu riga da wando ya dauko Blank and white ne,ada yaso sanya kayan agabanta sai wata zuciya tace"Saleem in har ka bari yarinyar nant taga girmanka toh daga yau shikenan ta gama rainaka gwara ka Rufama kanka asiri kaja girmanka.."Jin hakane yasa ya kwashi kayanshi ya Shige tiolet yana wata waka na " _Babe i love u,...Babe i kiss u..Babe i need u...._" Da kallon mamaki ta bisa tana gimtse baki,bai dade ba ya Fito daidai sanda Ummi tayi Knoking din kofar kafin ta turo,Da Malika taci karo zaune inda ta barta,cike da mamaki take kallon Saleem dake tsaye yana faman gyara Botiran gaban riganshi,Ganin tana mai wani kallo ne, yasa ya gimtse Fuska yana Fadin"Ummi menene naga kina hararata,ko haryanzu baki bar jin haushina bane..? Dakuwa ta sakamar tana Fadin"Kaniyarki da Ummi,don mai garinku kumo ina Abunda na sakaka.."?Tura baki yayi kamar yaro yana Fadin"Toh Ummi don Allah bayan na hadamata ruwan wanka so take najata bayin nayi mata? itace inaga bata ra"ayin wankan.."Yafada yana zakuda kafada. Haushi yakama Ummi ta kalli malika tana Fadin"Diyata ya baki tashi kinyi wankan ba.."?Kwalkwal malika tayi da ido zatayi mgana suka hada ido da Saleem yako zabgamata harara yana kada mata harshe ganin haka yasa Ummi ta kaimai Duka akeya tana Fadin"Fice kaban waje Maketacin miji kawai.."Dafe kansa yayi yana kallon Ummi kamar zaiyi kuka kafin yace"Kai Ummi,yanzu ni ace kamata  ban girmi da fada da duka ba? kuma ma wai agaban wannan yarinyar,plz Ummi don Allah  kidaina min Fada agabanta sai kisa ta rainani aie.."Yafada yana hade rai kyace wani ubanta. Tsaki Ummi taja tana Fadin"Shin zaka ficemin ne,ko kuwa sai na nuna maka kalata yanzu nan..? Juyawa yayi yana Fadin"Meye Zafi lauyan Abbi,Allah baki hakuri Ummin Saleem da marwan,da munafukar nan Saleema.."Dariya ta kama Ummi ammh sai danneta har yafice ya Rufo musu kofa. Maida kallonta tayi ga Malika tana Fadin"Meyasa baki shiga kinyi wankan ba dota.."? Dukar dakai tayi kafin tace asanyaye"Ai bansan ya hada bane,bai Fadamin ba Ummi.."Mirmishi Ummi ta mata tana Shafa kanta tace"Ok tom Shikenan barni dashi,yanzu tashi maza ki Shiga kiyi wanka kizo kiyi sallah kinji ko..? Kai ta gyada mata tana mikewa,Hannunta Ummi takama har kofar bedroom din tana Fadin"Ki saki jikin ki kinji ko? nan zan kawo miki abincin naki,ko zaki Fita Dining tare damu..? girgiza kai tayi kafin tace"Bazan iya cin komai ba Ummi.. Kallonta tayi kafin tace"Meyasa.. ?Kanta na kasa tace"Ina son naci buh ammh ko naci Sai nayi amai.."Takarishe Fada hawaye na cikomata ido,Dafo kafadunta Ummi tayi cike da tsausaya tana Fadin"Ayy srry,sannu kinji haka kowacce uwa tagari ke Fuskartan,ki daure ki dinga ci ko yayane, saboda abunda ke cikin ki,kuma koda kinyi aman ko ba duka ba,wani zai tsaya kinji..? Gyada kai tayi hawayen nata na zubowa cikin so da kauna da tsausayinta ta sanya hannu ta sharemata kafin ta bude kofar bedroom din tana Fadin "Yi maza kiyi wankan ki Fito,kan kigama sallolinki na kawo miki Abinci.."Batayi gaddama ba ta Shigen makeken Tiolet din mai kama da Falo guda,bin ko"ina da kallo take tana jinjna tsarin bayin,ammh wannan ko rabi da kwatan tsaruwa da haduwan nata bai kai ba,wasu kwallah ne suka zubomata tasa hannu ta share,ko acikin bath din kuka tayi tayi kafin ma tayi wanka tana Tuna sanda tana Gida komai sai dai ayi mata,ammh ga yadda rayuwa ta maidata. Sai da tagama wankan kana ta dauro alwala ta Fito,daure da tawul,akwatunta ta bude ta ciro kayan shafanta ta shafa kafin ta nemi wata doguwar rigarta Red colour,ta sanya wanda take da budadden hannh,tana tufke gashin kanta ne Ummi ta Shigo dauke da kololi abinci bisa wani katon Tire mai girma,Tana ganinta ta washe baki tana Fadin"Yauwa kefa,kinyi sallah ne..? Girgiza mata kai tayi tana dukar dakai,Gefe Ummi ta ijiye mata katon Farantin bisa cafet din dakin tana Fadin",Toh maza kiyi kizo kici abinci kada ki zauna da yunwa kinji ko.? Gyada kai tayi kafin tace"Tanque Ummi.."Mirmishi Ummi ta mata kafin tace"don't kinji..Is my Duty..."Daga haka ta Fice daga dakin. Ajiyar zuciya ta sauke aranta tana Fadin"Zuciyar iyayansa mai kyau,ammh shi ko ina ya gado bakin hali oho.."Bata gama mamaki ba ya sawo kai dakin waya makale akunnenshi yana waya,bai kalli inda take ba,illah Fadawa dayayi bisa makeken gadonsa yayi Ringigine,yana cigaba da amsa wayarsa,da ga duk alamun yadda yake mganar zaka san wanda yake wayarshi dashi bayi da wani muhimmanci saboda yadda yake bada amsa ayangance daga baya ma tana ji ya yanke kiran yana sakin wani Siririn tsaki. Tsayawa tayi kyam tana kallonshi daga saman Fuskarshi zuwa kirjinsa,yadda ya Lumshe idanuwansa kamar mai barci bayan ya goya duka hannuwansa bisa kirjinsa,ta Zurfafa da kallonshi tana yaba kyau da tsarin Fuskarsa bata ankara ba taga ya bude idanuwansa ahankali yana kallonta,Daburcewa tayi tana Zare ido kamar wacce tayi karya Bai mata mgana ba,illah juyamata baya dayayi yana Sauko da kafarsa daya bisa cafet din dake dakin,ganin haka yasa ta jingina da wardrope din dakin tana sauke wasu tawagen Numfashi,Ta hanzari ta dauki hijabin data cire,ta saka bata san gabas kawai ta tari yammah ta tada sallar tana ta buga Shirmen data saba.   Kamar ance ya waiwayo,sai yayi mugun gani,Ware ido yayi yana kallonta tana sallah,na farko ba gabas take kallo ba,na biyu wlh bakinta baya motsi baijin tana karantana wani Abu,daga sujjadan har ruku"un yi kawai take kamar wacce take dukawa tana duba wani abu,bai gama mamaki ba yaga ta zauna tahiya tayi Shuru kawai ta kurama waje daya sai chan kuma ta sallame,kara mikewa tayi zata kabbarta wata sallan da hanzari ya diro daga kan gadon sai gashi gabanta da kakkausan murya yace"Ke tsaya da sallar nan naki don Allah..." Yafada yana tsareta da ido,ba alamar wasa,jagale tayi atsaye tana raba ido,Habansa yakama da hannu yana Fadin"Ke yanzu sallar me kikayi..? Kanta na kasa tace"Na Azahar.. Jinjina kai yayi kafin yace"Ammh dai baki karanta Fatiha da sura ko? don naga ko minti daya bakiyi kike dukawa..? Dagowa tayi tana kallonshi ganin yadda ya tsareta da ido ne yasa ta sadda kai cikin sanyin murya tace"Fatiha kadai nake karantawa.." Dan ware ido yayi kafin yace"Why..?ko bakisan raka,"a biyun Farko Fatiha da sura bace,sai a raka'a biyun karshe ne zaki karanta Fatiha kadai.."Jim tayi kafin tace"Menene Sura,Ai ni d only Fatihan na iya.."Baisan sadda ya sauke ahannunsa ahaba ba yana binta da kallon mamakin kin Wuce Tunanina,jin shuru yasa ta dago tana kallonshi ganin yadda yake kallonta kamar na rashin hayayyaci yasa taji jikinta yayi sanyi sosai,nan da nan idanuwanta suka cika da kwallah. Bai samu zarafin mata mgana ba, saboda mamakin dayakeyi kai tsaye yasake jefomata tambaya"Guda nawa ne Farillan alwala,kuma nawa ne Sunnoninsa..? Bata dago ba,taji hawaye sun taho mata bata taba nadamar rashin ilimin addinin ba irin na yau,in da ta iya data ba Saleem amsa koda ta muzantashi kamar yadda yayi mata,sai dai kash bata san komai ba. Ganin tayi Shuru yasa ya bude baki yace",Shima baki sani ba ko..?Kai ta gyada mai ahankali tana kokarin maida kwallar data kusa zubomata,baki ya rike yana binta da kallon Ina da aiki,kai tsaye ya sake cemata"Ke wai tsayama,Kina wanka inda Janaba ta sameki,ko kuwa kina tsarkake kanki inda kin gama jinin al"ada..? Yafada yana kara saka mata ido kur yana kallonta. Tsuru Tsuru tayi da ido tana kallonshi kafin ta sadda kai kasa tana wasa da gefen hijabinta,Miyan bakinshi ne yaji ya kafe,saboda yadda yaga yanayinta bama sani tayi ba,mikewa tsaye yayi yana goya hannunshi abaya yace"Tambayarki nake ki sanar dani in baki sani ba,kada ki cucu kanki..? Kanta na kasa tace asanyaye"Eh ni bana kowani wanka,sai wankan da kowa yakeyi kamar wanda kayi yanzu ko bashi ba..? Ware ido yayi kafin yace"Na bani ni jikan Hafsat...Kina nufin kice ko Jini kika gama baki wankan tsarki? balle ma na saran ranar dana kusance ki bayan kin dawo hayyacinki kin Tuna  dayin wankan Janaban? Yafada idanuwansa sun Chanza launi. Kasa kawai tayi da kafafunta tana dukawa kanta na kasa ta Furta.."Wlh bansa komai ba,ban iya bane danayi,..."Tafada hawaye na zubar mata kamar an bude Famfo,kugu yakama yana kallonta,kawai sai wani shashe na zuciyarsa yatsausayamata matuka na yadda tana yar musulma ammh bata da sani kan Addininta. Ajiyar zuciya ya sauke yana Fadin"Is ok..Kina so na koya miki Karatun Addini..? da hanzari ta gyada kai tana Fadin"Eh plz...",Bai mata mgana ba illah Mikamata hannu dayayi yana kallonta,itama kallonsa take kafin jiknta asanyaye ta saka hannunta bisa nashi ya mikar da ita,yana jaye da ita har cikin tiolet din bai Direta ko"ina ba sai bakin Sink yana Fadin"Sake alwalan ki nagani..? Batayi gaddama ba ta duka ta sakeyi yadda ta iya,Girgiza kai kawai yake domin ita kanta alwalan bata iyata ba,haukanta kawai take,Baya yayi da ita kafin ya fara nadadde hannun Rigansa yana Fadin"Juz wacth me verg well kinji.."Gyada kai tayi tana kallonshi yana alwala,sai da yamayamata sau uku kana ta sake yi sau Daya,normal kamar yadda yayi mirmishi yayi mata yana Fadin"Tafiyanmu zata daidaita matukar kina da saurin Fahimta. Haka suka koma Dakin,da zuciya daya yake koyamata sallah yana mata bayanin komai daki daki,bai samu damar koyamata wani abu ba,sai da yasata ta rama duka salollinta,Isha"i ne kadai yaja musu jam''i bayan sun idar ne ya kalleta yana Fadin"First abunda zamu fara,shine gyara sallanki,yanzu gobe zan saka asiyo miki Karamin Qur"ani izifi biyu,Da Sauran kananun littafin da zasu taimaka miki,yadda zaki fara gane komai daki daki,ammh yanzu kici abinci kizo na fara koyar dake Abun ake Fada yayin Sujjuda,da kuma yayin Ruku"u zaman tahiyan farko da zaman tahiyan sallama.."Gyada kai cike da gamsuwa sai ta samu kanta da furtamai"Tanque...", Bai kalleta ba yace"No godema Allah.."Kallonsa tayi araunane batace komai ba,tashi tayi ta isa ga farantin da Ummi ta kawo mata,Kolan Farko ta bude ta iske White rice,sai kula ta biyu kuma Miya ne wacce taji kazi,kadan ta diba ta Rufe sauran,taji dadin abinci sai da cinye wanda ta diba duka harda kari,tasha Ruwa,yau anci sa"a batayi ammh ba,nan ta bar komai awajen,ammh takasa tashi,tana Tunanin kamar bai kamata tabar komai awajen ba,sai ta tuna tana gida Hajiya ke daukemata ko Su Dose da merry,. Satan kallonshi tayi sai taga baya tatata,domin hankalinsa na kan wayarshi yana Faman latse latse,sai lokacin Ta tuna da nata wayar,batama kunnata ba sai gobe,ganin yadda tayi Tsuru awaje dayane yasa yace"Kinga malama in zaki so na koyar dake kizo,in muka kina ganin zai zama takura zan kwanta ne..",Jin haka yasa ta mike da hanzari ta isa gabanashi tana Fadin',Gani ina so plz.." Tashi yayi daga kishingiden dayake akasa yana tankwashe kafa,tun kafin yayi mata mgana ta tankwashe kafafunta itama,kallonta yayi yana nazarinta kafin yace"Kina bukatar Abun Rubutu,ko hakan daliban ilimi ke zuwa.."Wiki wiki tayi kafin ma tayi mgana ya tashi ya dauko mata wani karamin joter da Pen,shikuma ya bude Dirowan gadonshi ya dauko karamin Qur'aninsa izihu Sittin ya bude yana Fadin"Fara karantamin Fatiha tukunnah naji.." Gyara zama tayi tafara karantamai yadda ta iya,Sai da tagama kana shi ya sake biyamata cikin Taushin murya da kira"a mai dadi,yayi mata gyaran sosai acikin nata karatun,sai da yayita maimatamata kafin yafara karantamata tana amsawa,bai kyaleta ba sai da Fatihan ta zauna bisa kanta sosai,kafin ya karbi Joter din daya bata ya Rubuta mata abunda zata Fada yayinda Sujjuda da Ruku"u da yayin Zaman tahiyan farko data karshe,wato Tahiya da salatin Annabi ya mika mata yana Fadin"Ki rike wannan,kidinga bita har ya zauna miki,zuwa gobe zan fara biya miki kananun Surorin kinji ko..?... Karba tayi bakinta na motsi bai bari tayi mgana ba,ya mike yana shafa kanshi ya Fada tiolet,Itakuma sai ta samu kanta da bin bayanshi da Kallo kafin ta Furta ahankali"He is so nice...",Tafada kafin ta mike tana Fadin"Alhamdulillah na samu *MALLAM*..."Ta fada tana jin dadin Abun har ranta,Jotern tayi ta dubawa tana zaune gefen gado,dayake yayimata Rubutun cikin kalmomin hausa,ammh kuma da Turanci yadda zata gane sosai. Har yafito tana zaune awajen alwala ya dauro yazo ya Shimfida darduma ya fara shafa'i da Wuturi,tun tana bin karatun har tafara hamma,saboda gajiya batasn sadda ta sulale bisa gefen gadon tana barci ba,shine daya idar da sallahn yazo ya gyaramata kwanciyar ya rufamata blanket,Shikuma bisa sallanyan ya yada Filo ya kwanta bayan ya Tube rigansa dagashi sai dogon wando don baya Hunce gaban yarinya ba ta rainashi,joter nata ya adana mata saman Side drower din gadon,addu"a barci yayi ya kwanta bayan yayi kasa da Hasken dakin ya kunna Dumlight. *WASHE GARI* Yau Saleem bai samu Fita masallaci sallar asuba ba,saboda malika,bayan ya jasu sallar sun idar yayi musu addu"o'i sai ya dauko Qur"aninsa ya biya mata Sura daya,Suratul Nas,yayi ta nanata mata harya zauna mata,sai kuma ya koma kara nanata mata Abunda ya Rubuta mata jiya,shima sai da ya tabbata ta iya wasu,babu laifi ya lura kwakwalwarta naja,tana da sharp brain sosai yarinya,ya yabamata ta wannan bangaren. Basu tashi daga karatunta ba sai da ya sanar dani yadda addini ya koyar damu mu"amala da mutane,ya sanar da ita babu kyau yima wanda ya girmeka rashin kunya ko mgana gatsal,kana ta koyi mu"amala da mutane da kuma girmama Manya,kuma yana daga cikin al"adun mu na hausa Fulani taimakon manyanmu,da koda munga suna wani aiki,yana daga cikin tarbiya sakaya sunan wanda ya girmeka ko ya kusa haihuwanka koda bai haifeka ba din,Kuma ya sanar da ita babu kyau girman kai,ko izigilanci duka haramun ne,zalunci Allah yahana kanshi kuma muma bayinshi yahanemu da yinshi,daga karshe ya sanar da ita Tayi Istigifari ga laifinta na baya Allah gafirun rahimun ne. Jinjina kai kawai takeyi tana jin dadin mganarshi,balle yadda yake mata mgana cike da dattako ne da kuma jarumta babu alamun sanayyah kawai yana koyamatane don taimakonta,daganan yace su dakata da karatun sai anjuma da daddare zai dora mata daga Abubuwan da suke wajabta wanka,da kuma shi kanshi wankan.." Yana kokarin tashi ne ta katseshi ta hanyar cemai " *MALLAM..* Ina da tambaya...? Yajita sarai ammh sai ya barsa wayarsa ya laluba yana kallon lokaci kafin ya waiwayo yana Fadin"Ba sunana Mallam ba,kirani da Saleem dina kai tsaye.."Mirmishi ta sakarmai mai taba zuciya wanda sai da ya tsaya yana kallonta. Motsa bakinta tayi tana Fadin"Nasani ba sunanka Mallam buh awajen malika kai Malamina ne,wanda yake kokarin tsamoni daga duhu zuwa haske,Ina da mahaifina ammh bai tsaya ya koyar dani yadda zan samu aljannata ba,duk da ban tashi hannun duka iyayena ba,ammh duk da haka bazan ki jinjinama Daddyna ba,domin shi yayi kokarin min gata wajen Tilastani aurenka,Bansan da wani baki zan godemaka ba mallam buh komai miye ina maka fatan Allah ya baka mai saka maka Fiye da yadda kamin.."Tafada hawaye na gangaro mata. Jikinsa ne yayi sanyi sai yayi saurin komawa ya zauna gabanta yana Fadin"Kin yarda ni malamin ki ne,wanda zai koyar dake hanyar tsira..? gyada mai kai tayi tana sharbe hawaye.,Daure fuska yayi kafin yace"To yazama dole duk Abunda nace kiyi do it ba gardama,? ta gyada kai kawai alamar gamsuwa,jinjina kai yayi kafin yace"Kizama daliba mai biyayyah da niyyar Neman ilimi,kuma mai biyayyah akowani lokaci,sai kiga Allah yabaki nasara kan Abunda kike nema.." Gyada kai tayi tana Fadin"Insha Allahu mallam,ngd sosai god bless u..."Cije baki yayi yana Fadin"Yi tambayarki,barci ne a idona..? Dukar dakai tayi tana Fadin"Dama game da abubuwan dana aikata abayane,shine nake tambaya,duk Allah zai iya yafemin..? Mikewa yayj tsaye yana gyara zaman jallabiyan jikinsa yake Fadin"Mezai hana,kin manta karatuntunmu,abaya na sanar dake Allah gafirull rahimu ne,so kiyi tuba zuwa garesa tare da Alqawarin da kuma yakinin bazaki koma ga zunubin ki na baya ba,ki kuma yawaita istigafari,Allah shi kuma zai Yafe miki.."Yana gama fadin haka ya haye gado yana lumshe ido,don har ga Allah bayanshi ya gaji da zama. Itako nan ta zauna tana bitan karatun daya koyamata,sai da tagaji don kanta ta hakuri itama nan bisa sallanyan barci ya kwasheta,bata Farka ba sai da taji Ummi na tashinta,kuma lokacin wani zazzabi mai zafi yagama Rufeta ko iya bude ido batayi saboda zafin jiki,goshinta Ummi ta dafa tana salallami,fita tayi taje ta sanar ma Abbi,shikuma ya kira Saleem wanda already ya dade da Fita Malika dai ranar haka ta Wuni da zazzabi,Hajiya babba ne tace ita irin cikinta kenan zazzabi da kuma amai domin wunin ranar hararwa tayi tayi kome taci sai ya Fito,dole ta hakura da cin komai,sai da yammah ne Ummi ta mata tuwo miyar kubewa,sai gashi ko taci sosai kuma batayi aman ba,Wuni Ummi tayi ita da Hajiya suna dawainiya da ita,haka Abbi bini bini ya leko yana tambayan ya jikinta,ita dai taga gata a Duniya,sai da wajen yammah ne taji zazzabin ya barta ta Rarrafa tayi wanka,ta sauya kaya tayi sallar mangariba,Sai lokaci Saleem ya dawo daga cikin gari,kuma bai manta ba ya taho mata da Abunda yayi mata alqawari,Qur'ani izu biyu,sai Ahalari,sai Bagadadi,sai bari wa biba,da littafin koyan baki,dana koyan Rubutu duk ya siyo mata,ammh ranar basu samu damar karatu ba,don Tunda takara cin tuwon da Ummi tayi mata tayi ta kelaya Amai,sai kuma zazzabi Daga baya,duk rashin imanin Saleem sai da ya tsausayama malika ganin yadda take bari da jiki saboda zazzabi,sai gashi saboda halin datake ciki bai iya kwana akasan ba,sai bisa gadon ya kwana kusa da ita yana kula da ita,duk da basu hade da juna ba,kowa na gefe,sai dai in yaji tana hada hakora sai ya waiga ya mata sannu,ya maida kai kawai aransa yana ayyana jibi jibin zai koma bakin aiki bazai iya da wahala ba. Ammh sai me washegari Sai Malika tatashi garas kamar ba ita,sai kuma Aranar ne ta kunna wayarta ta kira Daddyta da hajiya suka gaisa sun dade suna mgana dashi yana ta kara bata hakuri da Umartanta datayi biyayah ga mijinta,ada taso ta sanar dashi tafara zama cikakkiyar mace mai daraja,sai kuma ta fasa ta Fiso ta bashi mamaki ne,har tabama su Ummi waya suka gaisa da hajiya binta cike da fara"a. Tunda taga ta Samu sauki sai ta dukufa kan duba bitan karatunta Tunda dazu da safe ya bata qur"anin daya siyomata hade da sauran littafan,yanzu surorin dayayi mata take so haddacesu,mganar sallan ta kuwa tuni babu abunda bata gane ba yanzu sai dan Abunda ba"a rasa ba. Zaman shuru ne yayi mata yawa adakin ta tattaro littafanta tafito Filo ta zauna sanye take da riga da wando na pakistan red and black,sai wani red vail data yane kanta dashi gefenta hajiya ce wacce ke zaune tana kallon Tibin dake ta dimi shi kadai,ammh ba fahimta take ba,wani lokacin in malika bata gane wani waje ba, ita take nunawa ta gyaramata ko ta tadata,Hakika Su Ummi sunji dadi domin ko bakomai ilimantar Da mace ma lada ne,balle kuma Abu ne mai kyau miji yadinga karantar da matarshi domin sunnar ma"aiki ne hakan. Ta dukufa abitar karatunta taji sallama daga saman kanta tana dago kanta suka hada Four eyes da mai kama da Saleem,sak sai dai ita tafishi manyan ido,da Dan kiba kadan, dauke da wata katuwar jaka,irin ta baya din nan,sai katon trolly dinta wanda take jaye dashi,kallon kallon sukama juna kafin saleema ta dauke kai tana yatsina fuska,wajen hajiya ta nufa ta fada jikinta tana fadin"Oyoyo hajiyata i miss u..." Need ur pryers...🚗🚗🚗 *Momyn ladingo*😘 *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *KURIKE GIRMAN AMANAR DANA BAKU,KUYI MIN ADALCI KAMAR YADDA NAYI MUKU KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*👏   *17* .............Rumgumeta hajiya tayi tana Fadin"Kai Saleemata,sannu da zuwa..." Saleema na dariya tace"Yauwa hajiya,ya gida..? Kewar gida ya dameni sai kuma muka samu dan break shine na taho gida.." Kafadanta ta dafa tana Fadin"Muna munsha kewarki sosai ma kuwa.."Mirmishi tayi mata tana mikewa daidai lokacin da suka sake hada ido da Malika,wacce tun kallon da Saleema tayi mata taji ta muzanta,Sai ta koma gefe ta rabe,kanta duke ta kurama littafin gabanta ido,kamar tana karatu nan ko, ba karatun take ba,Jikinta duk asanyaye. Ganin sun kara hada ido ne yasa Malika tace ma Saleema"Ina yini,sannu da zuwa.."Wani dirty look Saleema ta watsa mata kafin kawai ta dauke kai,don ta Shaida ta tantiriyar matar Ya saleem ce,domin Abbi ya sanar da Ya marwan duk Abunda ya Faru,shiko ya sanar ma da  gindin rasit,wato Sadiq,shikuma ya sanarma patner dinshi Saleema,wacce kwata kwata Abun bai mata dadi ba,ita fa bata ga dalilin Abbi na takurama ya saleem kan wata chan banza jinin arna ba. Ganin yadda tayi mata ne,yasa malika taji idanuwanta sun kawo, ruwa Hajiya ce taga Abunda ya Faru ranta bai mata dadi ba,ta kalli Saleema tana Fadin"Saleema bakiji Matar yayanki na miki sannu da zuwa bane..? Tabe baki tayi tana jan akwatunta take Fadin"Wace...? ta fada tana dan kallonta cike da raini. Ganin haka yasa Hajiya mika mata dakuwa tana Fadin"Uwarki ce.."Baki ta tura kafin tayi gaba tana Fadin"Au kefa hajiya,baki ma mutun kawaichin marmari wlh.."Tafada ranta bace,ganin an zageta kan wata banza. Da Ummi taci karo ta Fito daga kichen,Rumgumeta tayi tana Fadin"I miss u my Ummi.."Shafa kumatunta Ummi tayi tana Fadin"Likita na wasa da karatunta ko? baki da aiki sai tahowa gida.."Dan dira kafa tafarayi tana Fadin"Kai Ummi break fa muka samu na one week,kuma nayi kewaeku ne,shiyasa nazo ganinku.."Sakinta Ummi tayi tana Fadin"naga alama,toh baki tsayawa chan kiyi karatu? . Tura baki tayi tana Fadin",Kai Ummi,ga kayan karatuna na nan cike da jaka,.."Dariya Ummi tayi mata tana Fadin"Uwar zence,kinganki Saleema bamai kadake azence..",Itama dariyan ta kyalkalyalace dash tana Nufar hanyan dakinta tana Fadin"Kai Ummi,me kike dafa na mana ne..? Shiga kigani.."Ummi ta bata amsa,Yar dariya tayi tana Fadin"Wai ni banga Abbi ba,kuma banga Malalacin Acp ba..? Tsaki Ummi taja tana Fadin"ke wai bana rabaki da sha"anin saleem bako.? Sun fita shida Abbi.."Dariya Saleema tayi tana Fadin"Kai Ummi bafa ni na sakamai sunan ba hajiya ce gatan chan.."Tafada tana nuna hajiya. Hajiya ko datake da cikinta na Abunda tayima malika,kyabe baki tayi tana Fadin"Kwarai ni na samai sunan,ammh sai na kirasa ya amsa don dole,kuma koda yaji haushi ban dakuwa,ke kuwa wlh kika kirasa da wannan sunan dakaina zan umarceshi daya nada miki na jaki Tunda baki da mutumci.."Tafada tana kumfar baki,Bude baki Saleema tayi kafin ta kada ta Wuce dakinta tana Fadin"Tabdijam,gamdamemiyar budurwan,da sake kam.."Tafada tana Shigewa dakinta dake yammah da na hajiya.   Malika ko na jinsu duk Abunda ke Faruwa ammh kanta na duke takasa dago kanta,Hajiya ce ta kira sunanta tana Fadin"Malika kiyi hakuri kinji ko? ahankali zaku saba da ita,ita kebima saleem.."Mirmishin yake tayima Hajiya tana Fadin "Babu komai.."Tafada tana kokarin maida hawayenta,kara sunkuyar dakai tayi tana Tunanin rayuwarta abaya ta tabbata da adane da kudi aka hada Saleema akace tayi mata Abunda tayi mata bazata taba yi ba,ke ko kusa da ita wlh bazata iya zuwa ba,ammh gashi yanayin rayuwa ya chanza da ita,har ana mata duk cin kashin da"aka ga dama Ammh babu komai tayi niyyar Tuba ga Allah kuma bazata koma ga halayyyata ta baya ba. Tashi tayi ta tatarra littafanta takoma daki ta kwanta bisa gado tana kuka,saboda takasa rike zuciyarta waje daya tsausayin kanta duk ya lullubeta,sai da tayi kuka ya isheta kafin ta mike ta fada tiolet ta dauro alwala tazo tayi sallar azahar,Bata son sake Fita taje su hadu da Saleema ta kara Wulakanta ta,shiyasa tayi zamanta adaki tana cigaba da duba littafanta,. Har akayi sallar mangariba Bata fito ba,sai da Ummi taji ta Shuru ne ta Shigo har dakin ta isketa saman darduma tana duba karatunta,Har ga Allah Abun Nama Ummi dadi ganin yadda malika take maida hankali wajen koyon ilimin addini,Gefen gadon ta zauna tana Fadin"Dota Anata karatun ne..? Gyada mata kai tayi tana Fadin"Eh Ummi sannu da aiki.."amsa mata tayi da kai tana Fadin"Yayi kyau in kingama ki Fito Falo,yau mu taru muyi Dinner kinji.."Gyada mata kai tayi kafin tace"Toh Ummi.."Tashi tayi ta Fice ta barta nan tana cigaba da karatunta. Koda Malika ta Fito babu kowa cikin Falon sai Ummi dake kwaso kololin abinci ,tana ganin haka ta isa gareta Da Sauri tana Fadin"Sannu da aiki Ummi.." Tafada tana karban kololin ahannunta,sakarmata Ummi tayi tana Fadin"In kin kai wannan maza kije ki zauna kinga baki da lafiya kinji ko? mirmishi kawai tayi tana Fadin"La wlh Ummi naji sauki bakima gani Ba.."Tafada suna karisawa bisa Dinining din,duk yadda Ummi taso tahana Malika kin hanuwa tayi,tare suka Jera komai,sai alokacin Saleema ta Fito daga daki,cikin riga da sikat,Wayace ahannunta tana latsawa kallo daya tayima su Ummi da malika ta dauke tana tabe baki Ummi ce tace"Sarkin waya,sai yanzu kika Fito na shiga naga kina wayarki na fama.."Ashagwabe Saleema tace"Kai Ummi,ni fa da ya sadiq ne.."Tafada tana zama bisa daya daga cikin kujerun Falon,tana dariya,Kafin Ummi tayi mgana sai  gaAbbi yayi sallama yana sawo kai falon,bayanshi kuma Saleem ne yana sanye da wata danyar gezner Light blue,wacce taji kyau dinkin muhammed,da hulansa zanna bukar,kayan su matukar amsanshi fuskarshi babu alamar fara"a ko kadan,sai dai bai tamketa sosai ba. Da Gudu Saleema tatafi gareshi ta fadamai tana mai sannu da zuwa,Riketa yayi yana tambayanta yaushe ta dawo,tace dazu ba dadewa Saleem dake bayan Abbi hankalinshi na bisa waya yaji saleema ta fadomai tana fadin"Mai girma Acp."Ta fada tana Rumgumosa. Wayarsa ya maida aljihun yakama kunnan Saleema ya murde yana Fadin"Ke wai bakison karatu ko? baki da aiki sai guduwa gida,Allah sa wannan Semister akori wlh.."tanajin haka ta sakeshi tayi baya tana diddira kafa sai kuka tana Fadin"Wlh Ta Allah bataka ba,Abbi kaga ya saleem ko? wai za"a koreni daga faculty mu..? Abbi dake zama bisa daya daga kujerun falon,yake fadin"Tunda har shi yagama ba"a koreshi ba kema haka zaki gama insha Allahu.."Dariya takama saleem yadan dara yana kallon Saleema yana mata gwalo,Ummi ce ta kariso wajen ita da Malika wacce ke satan kallon Saleem,shiko ko barayin datake bai kallah ba. Sannu da zuwa Ummi tayima Abbi kafin Malika ta duka tana gaisheshi,cike da kulawa Abbi ya kalleta yana fadin"Malika,ya jikin ki? ya bakunta,hop dai babu wata damuwa ko?Girgiza kai tayi kanta na batace komai ba,Abbi yace"Toh masha Allahu,Allah kara lafiya,komai dai kike bukata,ki sanar da Umminku gatanan kinji ko"Wannan karon ne ta bude baki tana Fadin",Tom Abbi nagde sosai.." Mikewa Abbi yayi yana tafiya zuwa sama yake cema Ummi "Wai ina hajiya banji duriyanta ba..? Saleema tayi karaf tace"Hajiya yau fa adame take,sai Fada take da mutane,hardani yau ban tsira ba.."Karamin tsaki  Saleem yaja yana fadin"Wa.? ai wannan hajiyar ta Abbi ko ba"a mata komai kullim cikin Fada take,ita ko gajiya batayi."Abbi yawuce kawai baice komai ba saima mirmish dayakeyi.,Ummi tabi bayanshi tana ma su Saleem dariya da Fadin"Ku shiga hankalinku,wlh in tajiku yau ko Sarkin kumo bai isa ya kwace ku ba.." Falon ya rage daga Saleema sai Saleem da Malika,wacce ke gefe zaune arakube kanta duke,hanyar dakinsa yabi Saleem ta kirashi tana fadin"Ya saleem.."Waigowa yayi yana Fadin"Miye..? Yamutsa fuska Tayi tana kallon barayin da Malika take tana fadin"Ashe kuma Abbi ya matsa maka sai da kadawo da wannan watsatsiyan yarinyar gaskiya ban..."Kallon da Saleem ke watsamatane yasa tayi Shuru ta bakinta tana binshi da kallon mamaki Ransa kawai yaji ya baci da Saleema tacema Malika watsatsiya,ko banza shine shaidan Malika,domin shi ya fara saninta abudurwa,ko bakomai zai kareta saboda martabanta,barayin malika ya kallah,suka ko hada ido,idanuwnta cike da kwallah har suka zubo,tayi saurin sadda kanta kasa tana share kwallah,sai yaji zuciyarsa batayi dadi ba sam,. Hade rai yayi yana kallon Saleema yace"inji uban wa yace miki matata watsatsiya ce? Saleema wai yaushema kika rainani,am your mate dazaki tareni da wannan banzar mganar..? Ya fada yana kafeta da rikatattun idanuwanshi,Tura baki tayi tana fadin"Daga mgana sai cibi yazama kari.."Tafada tana juyawa zata koma daki,cike da Fushi yace"Saleema...!.. Ya kirata da karfi,cak ta tsaya kafin ta waigo tana kallonshi Hannunsa ya tura ciikin aljihun wandonsa yana Fadin"Maza go and tell her srry,yanzunan if kuma..? Yafada yana Kuramata ido,Saleema tayi tsuru tana raba ido,tanajin aranta wannan ai reni ne,ganin tana turamai baki ne yasa yafara takawa zuwa gareta yana fadin"Wlh in baki bata hakuri ba, sai na ci ubanki yanzu nan na tatttakaki awajen nan,kuma na hadaki da Abbi,stupit gal kawai..",Wani kunya Saleema taji da takaichi kamar tayi kwallah,jan kafanta tayi zuwa gaban malika tana fadin"Srry..."Kanta gefe tafada,Malika dake duke ta dago tana mirmishin yake,tace"Bakomai.."Tafada tana jin kamar ta rushe da kuka. Wani banzan kallon ya watsama Saleema yana fadin"Get away from here,and dis is d last zaki kalleta ki cimata zarafi in kuma baki ji ba,try me and see.."Yafada yana kada mata hannu,kuka yazoma Saleema ta kwasa da gudu zuwa daki tana kuka tsaki yaja yana Fadin"Munafuka kawai..Yafada yana juyawa zuwa dakinsa  ransa amatukar bace. Bayansa malika tabi da kallo tana jin wani iri aranta,Akwana biyun da sukayi tare,in tace bata shaku dashi ba toh tayi katuwar karya haka kurum takejin sha'awar kallonsa,sannan muryansa tana jefata cikin wani yanayi wanda takasa fassarashi. Tashi tayi tabi bayanshi zuwa cikin dakin,sai ta iskeshi yana Kokarin tada sallar isha"i,batayi sanya ba ta Fada tiolet ta dauro alwala tazo da hanzari tabi bayanshi yajasu sallar,suna idarwa tace mai zata biya karatunta,bai musa mata ba,tabiya shi ko tar babu gardama,Karamata da sura biyu yayi zuwa gobe,tunda yaga karatun nata yana sauri sosai,Ummi ce ta kirashi awaya tace su Fito Falo suyi Dinner,bai sanar da ita ba illah Ficewa da yayi yana Fadin"Ki zo Ummi na kira.." Hijabinta ta dauka,wanda tazo dashi don dai bata da wani,Koda ta fito duka iyalan gidan sun hallara bisa katon tibirin cin abinci,hajiya babba ce kadai bata awajen,may yau bata ra"ayin ci tare dasu ne,don yau kam hajiya tsiya takeji,Saleema na kusa da Ummi,inda Abbi ke gefenta sai Saleem dake gefen Saleema,Jikinta asanyaye ta karisa tunkafin taja kujera Ummi tace",Saleema gyarama Antynki inda zata zauna.." Wani takaichi ne ya kule dama bata Wuce da Abun da ya saleem yayi mata,Shiko yana cin abincinsa ko kallonta ma baiyi ba,balle ya lura datana jin haushinsa,Dkyar taja mata kujeran tana sakin wani Siririn tsaki,Zama malika tayi tana dan mirmishi kadan,Ummi dakanta tayi sarving dinta Tuwon Shinkafa ne miyar agun,wanda yaji manshanu da naman kan rago,Tun kafin ta fara ci taji miyanta ya tsinke,cikin Son cin tuwo taja cokali tafara ci,itako saleema na gefe tana Faman zabgamata harara,wanda data dago ido,Zata ganta tana mata wani kallo,sai dai ta maida kanta kasa kawai idanuwanta su ciko da hawaye,saboda ita bata saba da wannan rayuwar ba. Saleem yana gama cin abinci ya yagi tissue ya goge baki yana Fadin"Abbi gobe fa zan koma bakin aikina.."Abbi yana cin abinci ya ijiye yana Fadin"Masha Allah,har kun gama mana bakunci zaku tafi? Toh Allah kaimu.."Jin Abunda Abbi yace ne yasa yace"A"a Abbi nikadai zan koma,ai Ita tana nan tare daku.." Zuramai ido Abbi yayi yana Fadin"Miye dalili..? Kai tsaye yace"Toh Abbi nake ga kamar hakan shine daidai.."Ajiyar zuciya Abbi yayi kafin yace"Ko daya sai dai kace kai hakan ka tsara,toh don mai garinku in katafi ka barta anan wajen wa zaka kabarta..?"Wani miyan takaichi Saleem ya hadiye yana Fadin"Tare daku mana Abbi,kofa na koma kasani ba zama nake ba,toh sai naga data rinka zama ita kadai gwara na barta nan ko banza zata dinga ganin mutane.." Mirmishin su na manya Abbi yayi kafin yace"Ra"ayinka kenan Saleem,ammh ba gaskiya bane duk uzurin daka bayar bamasu mihimmaci bane mallam,ka dauki matarka kawuce wajen aikin ka da ita,kana da muhallin bawai baka dashi bane,....",Saleem yayi jagale yana jin wani takaichi kamar ya fasa ihu, ya bude baki zaiyi mganan kenan Abbi ya dakatar dashi da cewa"Kul..Karka kara cewa komai,ka dauki matarka ku tafi,fakat umarni ne ba shawara ba..",Yana gama fadin haka ya mike ya haye sama,Malika dake zaune jikinta duk yayi sanyi ganin yadda Saleem din yayi,ada in akace tabishi bazata ba,ammh ayanzu batason ya barta anan,saboda shine gatanta duniya da lahira kuma bazata so ya barta da saleema ba,don sai ta zaneta saboda yadda take wurgamata wani banzan kallo Ummi ce tace"Ai kaji Abunda Abbinku yace ko? bai samu zarafin mgana ba ya daga mata kai,maida kallonta tayi kan Malika tana fadin"Dota kina so kibishi..? dagowa tayi tana kallon Ummi,kafin ta maida kallonta kan Saleem wanda ya kafeta da ido yana kallonta cikin wani yana so yaji mezata ce,itako wani yanayi taji yana shiganta saboda yadda ya tsareta da manyan idanuwansa masu dauke da wasu surrika kanta ta dukar kafin ta gyadama Ummi kai,washe baki tayi tana Fadin"Masha Allah,tashi to kije ki Shirya kayanki,Da safe zaku wuce ko Saleem? Gyada mata kai yayi,yana mikewa bai kai da gama tashi ba Saleema ta ture kujera tana sakin wani wawan tsaki takama hanyar dakinta tana kunkuni,dukkansu da kallon suka bita na mamaki,Saleem ne kadai da malika su ka san dalilinta na yin gaba,Ummi ko ta dauka ko wani ne ya bata mata rai. Adan kaikaice yabi bayan Saleem da kallo,Ransa ya baci da Abunda Saleema tayi mishi,yanzu ko bashi ba,ko malika ai ba sa"arta bace kuma a al"adance tana mtsayin Antintane,ammh saboda ta rainashi shi takema tsaki,Tunda ni sa"anta ne,bai yi yunkura binta ba ya kada kai yabi hanyar dakinshi yana cije baki. Malika bata bi bayanshi ba,sai da taya Ummi suka maida Kayan da suka bata zuwa kichen,Ummi taso ta hana Malika wanke wanke,ammh taki,tace sai tayi hakan ta barta suka wanke tare,sunayi suna hira,Ummi na kara mata nasihan hakuri da rayuwa,da kuma hakuri da biyayyah da mijinta,sannan Ummi ta roketa alfarma kada bayan sun koma zamfara ta yada karatun data fara koya,tace zata sanar da Saleem yasata a mkranta islamiya na matan aure,wanda zai taimakamata sosai.. Hakika taji dadin Nasihan Ummi da shawaranta,ita kuma tayi mata alqawari zata sameta mai Bin umarninta,Ummi ma taji dadi tayi ta sakamata albarka,wanda Malika taji dadi harda kwallah,saboda Farinciki don bata taba samun saka albarka daga wani ba,bayan Daddynta,sai gashi Ummi na sakamata haka Abbi,ai ita babu Abunda zatace da Ahalin Kabir kumo,sai godiya da Fatan alheri.   Koda ta koma dakin ta iske Saleem kwance ya juya baya yana kallon bango,wayarsa kuma sai daukan Tsuwa take,ammh sai ya dinga saka hannun yana latsewa,ganin bai mata mgana ba yasa ta fada tiolet ta wanke baki kafin Ta fito,wajen akwatun nanta ta isa,tana kokarin budewa taji yana Fadin"Meyasa kika ce zaki bini..?baki tsoron irin zaman da zai gudana tsakani na dake..? Waigowa tayi tana kallonshi sai taga baima juyowa ba, Fuskarsa tana kallon bangon dakin kamar ba shine bane,yayi mgana.   Bayanshi ta kurama ido,tana jin wani sanyi na Shiganta,Kasa mgana tayi illah kuramai ido kawai datayi,bata ankara ba taga ya juyo yana mikewa zaune bayan ya jingina bayanshi da gado,ido ya zubamata yana kallonta,kunya ne ya kamata sai kawai ta duka tana kokarin bude akwatinta taji yace"Ina tambayarki baki bani amsa ba,kuma kin tsaya kina kallona..,?"Ya Furta yana harde hannuwanshi akan kirjinsa.. Tana duke tace mai"Armmm me kace..? Wani kallo yayi mata kafin yace"Bansani ba kina nufin bakiji ni ba,bansan rainin wayau fa..?yafada muryansa acunkushe,diridiri tayi tana kallonshi Shiko ya sakarmata idanuwansa kamar zai daketa dasu,Sunkuyar dakai tayi tana Fadin"Kawai bani so kamin nisa ne.."Ware ido yayi yana Fadin"Really...? Saboda mene..? Kanta na duke tace"Saboda bani son karatun dana fara ya tsaya ne.."Yamutsa Fuska yayi yana Latsa wayarsa datake ta neman Dauki,yana sakin wani kafirin mirmishi,yace"Ba gaskiya bane,ko bani ba akwai masu koya miki karatu,baga Ummi ba ga kuma hajiya ko Saleema,duk wanda kika ma mgana zai koyamiki.."Idanuwanta ne suka ciko da kwalla,sai kawai tajuyamai baya tana share hanci. Mikewa yayi yana Fadin"Kinsan wani Abunda baki sani ba game dani? na tsani muna mgana da mutum ya juyamin baya,ko kuma yayimin tsaki? i hate does wlh.."Yafada yana daga kiran dake shigowa wayarsa bayan ya Fice daga dakin. Ajiyar zuciya ta sauke tana bin bayanshi da kallo,agurguje ta saka rigar barcinta,doguwar rigace mai kalan ja da fari,hijabinta ta saka ta haye gado,ta lafe gefen datake kwanciya,Tun tana sa ran dawowarshu har wani barci mai dadi ya kwasheta bata farka ba,sai da taji yana tashinta da asuba,lokacin ma harma yayi alwala Sanye da jallabiya,yace tatashi tayi sallah ta shirya yana dawowa masallaci zasu Wuce. Wanka tayi kafin ta dauro alwala,sai da tayi sallah kafin ta shirya cikin wani riga da Sikat,Rigar Farace da digon baki,sai sikat din na roba ne baki,yana da budewa daga kasa,sai vail dinta baki wanda ta yane kanta dashi bayan ta daure gashinta da band,Tana cikin sanya takalminta ne ya Shigo dakin,tana ganinshi ta rankafa tana fadin"Gud mrnig mallam.." Mrning.."Kawai yace yana kallonta kasa,,kasa,kafin yace mata"Baki da wani kayane sai wadannan.."tana durkushen tace"Eh.."karamin tsaki yaja yana Fadin"Ok,.Kada ki dauki kayan duka juz akwatu daya ya isa,munje chan zansa adinka miki kayan mata mai mutumci.."Gyada kai tayi kafin tace"Tanque.."Bai amsa mata ya shige tiolet,ita kuma ta mike tana hada kayanta akaramin akwatunta guda daya. Baijima ba ya Fito daure da babban Towel,kirjinsa na Fitar da maikon Ruwa kallo daya tayimai taji gabanta ya fadi,saurin dukar dakai tayi tana jin wani sanyi sanyi na Shiganta,bata jira komai ta Fice daga dakin kamar zata kifa saboda yadda jikinta ke rawa,da irin kallon da Saleem yake binta dashi,batasan dalili ba,ammh da zarar ya samata ido,shikenan sai taji tana neman rasa natsuwarta. Tana Fitowa Falo babu kowa,kichen ta Shiga,nan babu kowa Ummi bata riga ta Fito ba,kila yau bata da zuwa aiki da wuri ne,dakin hajiya ta wuce suka gaisa,ta sanar da ita zasu tafi,tamata Fatan Allah ya tsare hanya,Sai da ta Fiti daga dakin Hajiya kana taga Ummi ta Fito,tana kokarin hada breafsat,gaisawa sukayi cikin girmawa,Fere dankali Ummi keyi Malika ta kariso zata karba,Ummi taki bata tace tabari kawai kada ta bata kyanta,suna cikin hakane sai ga Saleem ya leko yana Gaishe da Ummi,gabadayansu suka waigo,yana sanye da Suit Red and black,ya daure wuyanshi da bakin Tie,jakar brief case dinsa ne sagale akafadanshi yana duba agogon Fatan dake hannunshi ne yake cema Ummi.. "Ummi zamu wuce,ina da Meeting 12.."Wukar Fera dankalin ta ijiye tana Fadin"Da wuri haka saleem...? Fita yayi daga kichen din yana Fadin",Eh Ummi,bari nayi ma Abbi sallama,Ke dauko kayanki ki Fito mana.."Yafada yana haurawa sama,Ummi tace"Maza kije ki dauko kayanki,Saleem bayason jira.."Jikinta asanyaye Ta koma dakin ta jawo karamar akwatunta tana kallon dakin cikin kewa,littafanta ta manta da hanzari,ta Daukosu ta saka cikin aljihun akwatun ta Fito,koda ta Fito Abbi da saleem sun Sauko kasa, har kasa ta duka ta gaishe da Abbi ya amsa yana tambayanta jikinta,ita kuma Ummi kichen takoma da hanzari ta Daukoma Malika Dambun nama dayawa cikin wata katuwar roba,ta damkamata karba tayi tana ta godiya,A gurguje Saleem ya Shiga bangaren hajiya suka yi sallama har bakin mota suka rakasu suna saka musu albarka,sai da motarsu ta fita daga gidan kana suka koma cikin gida cike da kewa.   *********    ************   Wurgi tayi da wayar bisa gado,tana zuba tagumi hannu bibbiyu,Nadira dake gefe tana kwance Ruf da ciki tana Danne danne bisa system dinta ta dago tana kallon Zahra take Fadin"Wht happend best..? Hawaye ne suka cikamata ido,ta girgiza kai tana Fadin"Best baya picking call dina,Tun Shekaranjiya nake kiranshi yana yankemin kira.."Tafada hawayen na zubomata. Ture laptop din tayi ta mike zaune tana Fadin"Shine ya isa ya sakaki kuka..?Kara Narke baki tayi tana Fadin"Haba best,do u know how much i luv him? wlh inajin in ban aureshi ba zan iya mutuwa..?Tafada wasu hawayen nakara zubowa mata.   Cike da mamakinta ta karisa gareta tana Rike hannuwanta take Fadin"Kinga srry inaga baya kusa ne,kimai uzuri kibar kiransa har zuwa gobe,in bai kira ba,ni zan nemasa ta wayata,kinji..? Kan jikinta ta kwanto tana Digan hawaye tace"Sai dai gobe ki kirasa,saboda bazan iya jurewa ba har nan da wasu Awanni ba..'Kanta ta Shafa tana Fadin"Ok don't wrry i will try my best,kibar kukan hakanan,yans tabamin rai kinsani.."Tafada tana dagota ta share mata kwallah tana Fadin"Oya smile.." Nakwa nakwa tayi da Fuska alamar zata kara saka kuka,Saurin taro habanta tayi tana Fadin"Oya Smile aha..,Smile MRS SALEEM KABIR KUMO"Kamar ana tallar closeup,haka ta washe baki tana Rumgumeta take Fadin"Tanque my best.." _*Don Allah ku sakamin Mamata Acikin addu'o'inku bata da lafiya,kuyi mata Fatan Allah ya bata lafiya da darajan manzon Rahama sallallahu alaihi wasallam*_😰😭👏🙏 *Momyn Ladingo ce*😘 *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *KURIKE GIRMAN AMANAR DANA BAKU,KUYI MIN ADALCI KAMAR YADDA NAYI MUKU KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*👏 *18* ................Karfe goma da yan mintina Saleem ya shiga da motarshi cikin dan karamin flat din gidanshi,megadinsa ne ya rugo da gudu yana mishi barka da zuwa,bayan ya gaida Malika data ke Fitowa daga mota,tana bin dan karamin gidan nasu da kallo,duk da gidane daidai na talaka,ammh kuma ya burgeta sosai.   Saleem da kanshi ya daukan mata akwatinta zuwa cikin gidan,mai dauke da Babban Falo da 2 bedroom sai kichen,shikenan,ammh duka dakunan akwai kayan more rayuwa aciki,Dayan bedroom din ya kaimata kayan nata,bai mata mgana ba,shi kuma ya Shiga wanda Tun dama nan ne dakinsa,Bai dade ba ya Fito ya Fice daga gidan gabadaya bayan ya sanar da ita ta shiga ciki Shi zai Fita. Malika ta dade zaune afalo tana bin ko"ina da kallo kafin,tatashi ta shiga dakin daya nuna mata,shima din ba laifi,Tunda yana malale da wani makeken cafet,ja sai Gado da wardrope sai dressing morrior dinshi,sai Kofar tiolet,Dakin duk yayi kura sosai alamun andade ba"a Shigo shi ba,hankalinta ne yatashi ta rasa ta ina zata fara gyara dakin ita daba komai ta iya ba,Ta tuna sanda tana Asalin malikarta,wlh ko baranta bazai zauna awannan gidan ba,ammh gashi rayuwa ta juya da ita,itace zatayi rayuwa awannan gida,kuma batare da wasu yan aiki ba. Hawaye suka cika mata ido,tayi zaune gefen gado tana goge hanci,ganin zama ba nata bane,cuz Malika bata son zama cikin kazanta mikewa tayi tafara kakkabe dakin tana gyarawa,sai gashi har kayanta ta zazzage daga akwati ta jera cikin wardrope tanayi tana hutawa,tana tunawa da merry da Dose,tana gode musu aranta,wanda ko dauko kaya batasan wahalanshi ba, Koda tagama gyara dakin wanda harda tiolet ta wanke,don bazata iya wanka dashi ahaka ba,bayan ta ya kage,dakyar take mikewa,Falo kuwa sai da tayi hawaye wajen shareshi,kichen dai ko kallonshi batayi ba da dakin Saleem don koda tagama tafita hayyacinta,wanka tashiga tayi,saboda tsabar jigata azaune tayi sallah Azahar da la"asar alokaci daya saboda jirin data ke gani,Ashe harda yunwa sai lokacin ta tuna duk Wunin yau bata ci abinci ba,Jingina kanta tayi jikin gadon dakin tana tsiyayan hawaye,tana tuna yau fa in kaine to ka tabbatar da zuwa gobe waninka ne,Itace fa *MALIKA MALIK* abaya mace ce,mai aji da jinkai,ilimi da takama,In tagama sai tace bazataci abinci kasar Nageria ba kuma ta zaunu,Bata cikakken sati a kasa daya,ammh sai gashi yau ankoma itake rabe awannan gidan tana kukan Yunwa da gajiya,wayyo rayuwa kenan.. Haka take ta zencen zucci har barci yafara kwasheta babu Saleem ba dalilinshi,kiran wayartane ta farkar da ita daga barcin data fara nan kan Darduman,Zabura tayi ta mike ta dauki wayan wanda ke kan Stool din gadon tana neman Dauki,sunan Daddylove dinta tagani yana kiranta da hanzari ta dauka,tana gaisheshi amsawa yayi cikin murna da Farinciki kafin ya tambayeta iyayen mijinta da shi mijin nata,amsa mai tayi duk suna nan lafiya,nan take sanar dashi yau suka zo zamfara,yaji dadi sosai yayi ta sakamata albarka,jikinsa ta tambaya da kuma hajiya,yace komai lafiya,kafin yabama Hajiyar waya suka gaisa,tana kara jadaddamata data kula da kanta da Abunda ke cikinta,gyada kai take cikin zuciyarta tana kukan zucci. Bata karajin kuka ya ciyota ba,sai da Daddy ke tambayanta taci abinci,wasu hawaye ne masu zafi suka ketomata,bata samu zarafin sharewa ba,tabarsu suna ta sauka bisa hijabin dake jikinta,dakyar ta furta eh taci saboda batason Ta fadi wani Abunda zai tadama Daddynta da hankali wanda bata da kamarshi duk Duniya,domin shine gatanta yanzu,koda suka yi sallama Daddy yaso ya fahimci wani abu game da ita,ammh ta tabbatarmai da lafiyanta kalau kuma babu Abunda take bukata. Itako Zuru tayi bayan sunyi sallama,tana tuna lokacin tana gida,sai taga dama ma takecin abinci,in bataci ba ko Daddy ya dinga rawan jikin lallashinta taci abinci,in ko iskacinta yatashi sai tace duka abincin basu mata ba,sai ansake dafamata wani,Watarana ma ko andafa sai tace bataci ta dauki mota taje wani Restaurant taci abincin data ga dama,ammh gashi tana neman abincin ma taci basai ta jira an lallasheta ba,ammh bata samu Ba,Saleem yayi tafiyarshi ya ma manta yazo da wata halitta wai Malika. Shiko Saleem Tunda ya Fita bai zarce ko"ina ba sai headquater su,meeting din daya tara suka shiga,sai wajen 3 suka Fito yafada office, yana shiga office ya tarda tarin Cases cases,kala kala nan yazauna yana dubasu kwata kwata bai samu sukunin kanshi ba banda sallah babu Abunda ke tadashi,kwata kwata ya manta da wata halitta malika,sai da Ummi ta kirasa tana tambayan ko sun isa lafiya,kuma ya turomata nombar Malika zata kirata ta mata Allah huta gajiya."Sai alokacin ya saki salatin aranshi yana dafe kai,koda ya duba agogon Shidda saura na yammah,da hanzari ya Fice daga office din yana jin ransa babu dadi in bai manta bata karyaba gwarashi ma dayazo Office yasha tea,ammh itafa bataci komai ba,Tun safe ga kuma ciki,kai ya illah nan da nan yaji bai kyauta ba, gaskiya. Agurguje ya isa wani Restaurant yayi mata take away din Fride rice,da ferfesun kayan ciki,sai lemon hollandian da Viju,don yaga ko agidansu tafi sonsu sosai,koda ya isa gidan Abun gwanin ban tsausayi,ashe da yunwar ta isheta Sai ta tuna da dambun namanta wanda Ummi ta bata,shi ta dauko ta dinga ci babu kama hannun yaro,toh shine ma man Gyadan suyan Dambun naman ya dinga Taso mata,sai amai tun tana iya tashi ta Shiga bayi har daga karshe takoma tana kelayashi akasan cafet din dakin,koda ya Shige ya isketa kwance cikin amai tana maida Numfashi ga dambun naman ne agefe aroba taci fiye da rabi da kwata,Hankalinsa tashe ya duka gabanta yana Fadin"innalillahi,ke me kika ci haka..',? Yafada yana binta da kallo,nan idonshi yabashi amsa,ganin robar dambun naman,ido ya zaro daya tuna yawanshi ammh saura kadan,Dawo da kallonshi yayi kanta ganin yadda hawaye ke Fita idanuwanta sai da yaji tsikar jikinsa ya tashi,Cikin wani yanayi ya Furta'"Dole kiyita amai kalli uban Dambun da kikaji haba,shikenan bazaki dinga kiyaye lafiyanki ba,Tunda kinsan halin dakike ciki.." Bata iya dagowa ba,dakyar ta iya Furta"Yun..wa...Na..ji..",Tafada tana Sharbe majina,Wani tsoro ne ya shigeshi ganin tana kara dago ido sama kamar zata shide,da hanzari ya ijiye lodojin daya shigo dashi ya kama hannunta ya ciccibeta tsab ajikinsa ya nufi hanyar Toilet da ita yana Fadin"Am srry sam na manta dake,koda naje office na tarar da tarin ayyukane,su suka daukemin hankali,ammh da kika jini Shuru why not kikirani ta wayata..",Tanajinsa bata iya bashi amsa saboda wani Haushi ma,daya kamata ita ina taga nombarshi balle ta kirashi,Kalmar ya manta da ita tafi komai bakanta mata,ita take sata kwallah tanayi tana Sharewa da hannu.,sauke ta yayi tayi saurin dafa bango ta tsaya kan kafafunta. Da kanshi ya hadamata Ruwan wanka,ganin ya Nufota,da hanzari taja baya tana fadin"Zan iya yi da kaina.."Bai damu ya tabe baki yana Fadin"Ok.."Daganan ya Fice daga bayin,yana Fita tabi bayanshi da kallo tana Sakin Siririn kuka,Tanajin takaichi yadda yanzu komai na yaron yake burgeta,tanajin gwara ta zauna dashi Fiye da kowa ayanzu,dakyar ta iya shiga bath din ta gasa jikinta,ammh tanayi tana kukan makomar rayuwa,yanzu balle ma nan gaba. Sai gashi Saleem ya nadadde kafan wando hannun Riga,shi ya goge aman datayi Tas,kamar bata bata wajen ba,Duk da babu wanda ya kaishi kyamkyamin amai,Aranshi yasa ne kawai don shine silan Shiganta wannan Halin ya barta da yunwa,da kar wani abu ya sameta Abbi da Ummi su tsinemai yabi Duniya,shiyasa ya zage ya gyara ko"ina,koda ta Fito bashi adakin ammh ya barmata sakon Take away dinta,kallo daya tayi ma take away din ta kauda kai domin Duk wani abinci ya Fitar mata aka yanzu,mai ta shafa tazo ta shimfida sallaya,ta nada mayafinta akai,Tunda hijabin ya lalace tayi sallar mangariba,bata tashi daga wajen ba,sai datayi sallar isha"i kana ta rarrafa ta hau gado ta kwanta tana ji kamar bayanta zai cire,Dakyar tasamu barci ya kwasheta. Shima saleem ya dakinshi yakoma yayi wanka yayi alwala ya fita masallaci nan gaban gidan ne,shima bai dawo ba,sai da yayi sallar isha"i,ya shigo mata da kaza kasassiya koda ya leka dakinta tayi barci duk ta kure,Ya dade tsaye yana kallon Fuskarta yadda duk ta rame kwana biyu,bai san dalili ba kawai sai yana jin tsausayinta yana Shiganshi duk da bayason tasirin hakan ya shigesu sosai,kauda kai yayi zai Fita,sai idonshi yakai kan Lodojin take away din daya yimata,ganin bata taba bane,yasa ya dauka duka harda kazan ya kaimata kichen ya bude fridge ya sakamata aranshi yana Fadin"Zaki nemeshi gobe,in baki ci yau ba.." Shima dakinshi ya shiga yayi shirin barci yafada gado,sai alokacin ya kara duba wayarsa,wacce ya bari agida misseds din Zahra ba adadi kai ya dafe aranshi yana Fadin"Allah ya hadani jaraba,kai yarinyarnan in mayyace takama mutum sai Allah kuma.."Tsaki yaja afili kafin ya latsa nombar ya marwan wanda hardashi a cikin wadanda suka kirashi baya kusa.   ******************** Washegari Saleem bai yarda yabar Malika da yunwa ba,12 nayi yaje yayo mata take away yakai mata,Tunda dai ba'iya girkin zatayi ba,koda ma zata iya yi bata iya dafa komai ba,so ko ma yace tayi zai batama kanshi lokaci ne,balle bata da wani issshiyar lafiya sosai,shiyasa ya dauki Nauyi kullun yayo mata takeway sau uku arana. Basu samu daman cigaba da karatu ba,sai da suka kwana biyu da zuwa kana yake dora mata da daddare,da asuba kuma ta biyamai,babu laifi Tafara sanin addininta da abubuwan daya kamata tasani,Kayan sawanta kuwa Sargent musa yayima mganar yanason Siyan Atamfofi da lesuna,da hijabai,da kuma inda za"ayimai dinkuna masu kyau,nan yacemai ai baya da mtsalan wannan matarshi tana Sana"ar Saida Atamfofi,gabadaya kwangilan Siyan kayan da dinkin ya tura mata ta acccoun dinta ita kuma ta siyan mata atamfofi da lesuna,aka dinkamata dinkin Riga da sikat,da masu zani,ko masurement dita,shi ya fasalta yadda take,saboda yana ji aranshi ba wani wawan Telan da zai bari yazo ya saka tep ya gwadamai matarshi.😂 Nadira kuwa tacika alqawari domin takira Saleem,ammh itama sai da tayimai 3 missedcalls,kafin ya daga lokacin yana office yana aiki,kanshi ya dau zafi,koda ya daga kiran Bai yi mgana ba ganin bakuwar nombace,Tunkafin yace komai Nadira ta gabatar da kanta amtsayin Cousin Sister din Zahra,yamutsa Fuska yayi yana asking dinta wacece zahra kuma? Amsa ta bashi da Fadin"Zahra bukar mada,sai lokacin ya tuna da mayyar yarinya,Tsuke baki yayi yana jin bayanin Nadira tana sanar dashi irin halin da Zahra ta shiga saboda shi,wai harda kuka baki ya rike yana Jinjina Abun,aranshi yana Fadin"Lalle yarinya kin zake dayawa.."Hakuri yabama Nadira yana sanar da ita Aiki ne yayimai waya baya samun lokacin kansa,ammh tabari zuwa anjuma in ya koma zai kirata insha Allahu,daga haka sukayi sallama ya kife wayar yana jan tsaki,haushi duk ya kamashi Afili ya Furta",Nayi kuskuren bama Yarinyarnan Digit dina wlh.."Yafada yana Sosa kunnenshi da pen din dake hannunshi. Itako Zahra agabanta Nadira ta kira Saleem, bayan ta saka wayar aspeaker,tana jin sanda yace zai kirata ta koma gefe tana tsallen murna,Suna gama wayar ko,ta daka tsalle ta Rumgume Nadira tana mata godiya,itako tana binta da dariya bayan ta zaunar da ita tana bata Wasu karin Sirrinka da zata kama zuciyar Saleem dashi itako tana gyada kai murna duk ya cikata,kamar ance gobe ne bikinsu. Shiko Saleem aranar bai koma gida ba,sai araound 10:39,yakoma agajiye Takeway din Malika ya kaimata fridge,saboda ya iske har tayi barci,Wanka kawai yayi dakyar yayi shafa'i da Wuturi,ya haye gado zai kwanta,wayarsa ya dauka zai kashe,sai yaga sakon zahra na yawo bisa saman wayarshi,yana ganin sakon bai kai ga Shiga ba alqawarin da yayi mata ya fadomai arai,bai karanta sakon ba ya lalubo nombarta wacce bai adanata ba,ammh tsabar nacin kiranta yasa ya ke gane Nombar. Zahra ko tana zaune dirshan akan gado tayi tagumi da hannu bibbiyu faskekiyar wayarta ne agabanta ta zura mata ido,fuskarta tana nuna tsantsan damuwar datake ciki,Nadira dake gefe kwance ta dago tana kallonta kafin tace"Wai don Allah best baki kwanciya kibar wannan damuwar..? Bata kalleta ba tace cikin Sanyin murya kamar zata fashe da kuka,..",Toh bai kirani ba best.."Ajiyar zuciya ta sauke kafin tayi mgana wayar Zahra dake gabanta ta dau tsuwa,koda ta kyallah ido taga Sunan Saleem wanda tayi Saving da *COOL EYES* da wani uban zabura da chakuma ta damko wayar ba inda jikinta baya rawa take Fadin"Best..best gashi yana kirana.."Mikewa zaune Nadira tayi tana Fadin"Dallah to ki dauka,kin zauna kina rawan jiki,har sai wayar ta katse.."Tana jin haka ta dauki wayan tana karawa akunne cikin sanyayyiyar muryanta ta Furta.."Hello..." Gyara kwanciya yayi yana Fadin"Hello kina lafiya.."Ya fada kai tsaye,Washe baki tayi kamar zatayi dariya,Hararanta Nadira tayi tana Mata mgana da hannu,da hanzari ta gyara muryanta tana Fadin"Lafiya lau,Fatan kaima kana cikin koshin lafiya kamar yadda nake..",Fuskarsa ya dan saki kafin yace"Normal..."Shuru ne ya biyo bayan kafin Saleem ya kauda shurun da Fadin"Dazu cousin Sis dinki ta kirani,duk da am very Sure,kina wajen ta kirani,so tayimin complain din kina kirana bana picking,do u know what..? Girgiza kai tayi kamar yana ganinta kamar yasani ya cigaba da fadin"Ban cika son yawan takura ba,ni mutum ne jama"a,kuma ina kokarin kare hakkin kasata,da kuma Tsoron rantsuwan danayi wajen sanya kakin yan sanda,so plz nd plz kidaina damuna da kiranki kina Shiga uzuri na sosai,ki bari ni dakaina in na samu lokaci i promise u i will call u.."Wani yamm Zahra taji idanuwanta suka ciko da kwallah,Ta juya tana kallon Nadira,wacce taji komai domin Zahra ta sanyamata aspeaker. Alamu tayi mata da hannun data bashi hakuri,Maida kwalarta tayi kafin tace"Ayyh am srry bansan cewa kulawar danayi dakai zai zama laifi ko takura ba,buh insha Allahu korafinka ya karbu za"a kiyaye.."Tana Fada tana yaken karfin hali,mirmishi yayi mai sauti ganin kamar mganarshi ta sosa mata rai,sai yadan saki ranshi yana tambayanta mutanen gidan,kafin ya gangaro yana tambayanta karatu,nan zahra ta tankwashe kafa tana bama Saleem lbrin matakin karatunta,dayake ta iya lankwashe murya,duk bawasu kalamai ta iya ba,Nadira ce ke dorata bisa hanya,Tunda ta Fita budewar ido. Sai gashi hira tayi dadi tsakanin zahra da Saleema,sai wajen 12 suka kafin suyi sallama,shima bawai don Zahra ta gaji ba,sai don Saleem ya nuna yana jin barci saboda Fita aiki gobe,itako Nadira tun tana jinsu sama sama har barci ya kwasheta,sai da zahra tatasheta tana ihun murna,tana sanar da ita yamzu suka gama waya da Saleem,Nadira ta rumgumeta tana ihu,wanda gar Momi dake dakin Abbansu,ta Fito tazo kofar dakinsu tana tambyansu lafiya,sai lokacin suka dawo hayyacinsu,Nadira ce tace wai Ya Nazir ne yayi musu kyautan 50k ta account yanzu,tsaki taja ta wuce tana Fadin"Allah ya Shiryeku kuyi dai ahankali yanzu dare ne.." Sai gashi duk dare sai zahra da saleem sunyi waya da juna kafin su kwanta,duk da yanzu ta rage kiranshi,ammh kuma ta chanza taku takoma turamai sakon soyayyah masu sanya zukata,wanda Nadira ke Rubuta mata tana turamai,na safe dabam na rana dabam hakama na dare shima dabam,kuma kalamai so sexy and Romantic,shiyasa lokaci kadan Zahra ta fara burge saleem,har baya iya barci sai yaji muryanta,duk da wani lokacin yana basar da ita,bayason soyayyarsu tayi zurfi kuma yazo yace zai aureta Abbi ya dakatar dashi. *BAYAN WATA DAYA* Wata daya kenan da zuwansu zamfara,Alhamdulillah kawai malika zatace domin abubuwa suna Tafiyan mata yadda Yakamata,duk da akwai abubuwan da ba haka taso ba,bangaren karatunta kuwa Tuni tayi nisa son Saleem bai yi mata da wasa,koyar da ita yake kamar yadda ya dau alqawari,bata aikin komai sai gyara dakinta da Falo in yayi kura,da yan kwanuka in ta bata,Mganar abinci kuwa Saleem yadauke mata wannan Nauyin nayimata takeaway kullum sau uku arana,kuma babu laifi yana bata kula sosai abangaren cikinta,ga kuma kayan daya kawo mata kamar za"a bude shago,ta dade bata iya daura zani ba,sai da ya dinga koyamata,ko daura dankwalin ma,shike amsa yana gwada mata yadda zatayi har tasamu ta iya dan sagala shi,ganin Riga da zanin na bata wahala sai takoma sanya masu sikat kawai saboda sunfi mata saukin sawa,duk tafi sati kafin ta saba da saka kayan,da farko damunta sukeyi ba kadan ba,sai hijabai wajen kala ashirin da masu hannu da marasa hannu,kuma duka yadi uku da rabi rabi ne,in tasaka har kasa suke kaimata kamar wata zulumbiya😂 Satinsu biyu da zuwa gidan ta samu ziyarar wata makociyarsu wanda gidansu ke kallo nasu,MAMAN ABBA,Nurse ce tana aiki general hopital Zamfara. Mijinta kuma manajan bankin First bank ne,danta daya Isma'il suna kiranshi Abba,Ta shigo suka gaisa da malika,nan take sanar da ita ga gidanta nan kusa da nasu,tun sadda Acp ya sanar da Baban Abba,cewa yazo da matarsa takeson Shigowa ammh kuma bata samu lokaci ba sai yau,fatan zasu dinga zumunci.... Murna ta cika Malika rana ta farko Tun bayan Shiganta wannan Halin ta samu wani akusa da ita,cikin Fara"a da sakin Fuska ta karbi Maman Abba,wanda suka dade suna hira kafin tayi mata sallama tatafi,da saleem ya dawo jikin Malika na rawa ta sanar dashi zuwan Maman Abba,tace kuma ya barta itama ta Shiga wajenta,murtuke Fuska yayi yace bai yarda ta Fita konan da kofar gida ba,Dole ta hakura duk da ranta baiso ba ammh bata nuna mai, ba,Wannan Abun yana sa Kimarta yana karuwa a idon Saleem sau tari zai kuntatamata da gangan ammh ko a fuska bata nuna taji haushi ko ranta yabaci,sai dai shi yadaga baya yaji bai kyauta mata ba sam. Maman Abba batayi Fushi ba dataga Malika bata Shigo ba kamar yadda tace sai ita ta Shiga wajenta,suka kara gaisawa,nan take kara lura da cikinta har ya Fito,ada kamar bazata tambayeta sai kuma ta tambayeta ko ta fara zuwa awo..? amsa mata tayi da"a"a.Nan,Maman Abba tace aiko yakamata kifara zuwa awo,saboda daga ganin cikin jikin ya kai 4month in ma baifi ba,Mirmishi kawai malika tayi tana sunkuyar dakai,don azahirin gaskiya bazata iya dora komai kan cikin jikinta,game da Saleem ba,don bata ga yana wani damuwa dashi ba balle dokinshi,balle har yagane ya isa zuwa awo. Bata mai mganar ba,sai da aka kwana aka Wuni,bayan sun gama karatun dare,take mai mganar zuwa awon da Maman Abba tayi mata ya dade yana kallonta domin shima satin daya Wuce Ummi ta kirashi take tambayanshi Malika ko tafara zuwa awo..?karya ya zabgamata yace eh kafin ya gyada kai yana Fadin"Yaushe ne tace zaki fara zuwa awon..?Kanta na kasa tace "Bansani ba,sai in ta shigo na tambayeta.."Mikewa yayi daga tsaye yana Fadin"No gobe da Safe ki Shirya ki shiga gidan sai ki tambayeta,ko goben zaki fara sai ki sanar dani.."Gyada kai tayi tana Fadin"ngd.."Bai kulata ba ya Fice daga dakin zuwa nashi,yana kokarin amsa wayarshi wacce zahra ce ke kira. Haka ko akayi da safe bayan ya tafi tayi wanka ta saka atamfanta dogowae riga da dogon Hijabinta ta Shiga gidan Maman Abba ta sameta tana Shiri zata asibiti yau Dutyn safe gareta,nan suka gaisa cikin Fara"a Shine take sanar da ita Abunda Saleem yace,Maman Abba tace "Toh ai Faduwa tazo daidai da zama,gobe ne ranar Zuwa awon ,sai ki koma ki sanar dashi,gobe in zan Tafi sai mutafi tare,Allah barshi bayan an miki scaning da sauran abubuwa,ni sai na cigaba da dubaki agida. Haka ta sanar da Saleem da daddare bayan ya dawo,bai yi gardama ba yabata kudi 10k yace taje dashi,da kanshi ya dauki wayarta ya saka nombarshi yace takirashi in ance ana bukatar wani abu,Murna takama malika ranar batayi barci ba tana murnan yau itama zata asibiti ta shiga sawun iyaye mata masu ciki,koda 8 tayi sun tsufa ageneral ita da Maman Abba,wacce ta tukasu asabuwar motarta 306. Sakamakon zuwanta da wacce take da sani awajen Bata wani jima ba,aka bude mata Fayel likita ya dubata kafin aturata dakin awo,Shima din bata jima ba Tafito,Aka bata sati hudu ta dawo,batayi amfani da kudin da Saleem ya bata ba,saboda asibitin ta gwannati ne,sai dai ta siya magungunar da'aka Rubuta mata na karin jini,Maman Abba da kanta takara tukota ta maidata gida tana ta mata godiya. Saleem yana office ammh kuma rabin hankalinsa na kan Malika yana so yaji ya ake ciki,gashi bai karbi nombarta ba,Ganin har wajen yammah bata kirashi ba,kuma yau bashi ya kaimata abinci ba, Sarger musa ne,ammh ya tabbatar mai da megadi yace ta dawo Zahra ce ta kirashi ta daukemai hankali da hirarta tana mai kukan Shagwaban yaki yazo ya ganta,Shikuma bayaso yayi mata alqawari ya saba ne,yau dai ya tabbtar da mata data jirashi zai zo dis weeked insha Allahu,Murna kamar zata kashe Zahra tayi ta murna tana tsalle ita da Nadira,wacce itace ke dorata adukkan hanya data kama Saleem yanzu ahannunta,duk da bai gama kamuwa duka ba. Shiko Saleem yanajin aransa zai iya maneji da zahra,domin yana cikin wani mayuwacin hali na bukatar mace akusa dashi,bayaso yaje ga malika tadauka yafara sonta ne,Ko ana Farko yayi mata hakane don tagane kuskurenta,yanzu kuma sai yakoma..? Abun da kunya gaskiya bayason yarinyar ta rainashi sam,ammh kuma yakasa Fuskarta wani abu koda zai ga mata awaje koda ko da wani irin banza Shiga ne basa burgeshi kuma bayajin hankalinshi ya tashi,ammh da zarar ya dawo gida yaga Malika,sai kawai yaji yanayin jikinsa ya chanza,ko dakinsa tazo karatu haka zai dinga jinsa konai nasa na chanzawa,In ya kalli cikin idanuwanta tsausayinta da sha'awarta na kara Tsumashi balle yanzu yadda ta cika sosai kirjinta da kugunta sun kara Fitowa,haka Fatar jikinta tayi kyau Fuskarta tacika da kumatu ta kuma kara haske Fata,koda kuskure jikinsu ya hadu da juna,ranar haka zai kwana mafarki sai Da asuba yayi wanka Kafin ya tafi mssallaci,Yarasa yadda zaiyi da rayuwarsa,Sai kawai ya yanke shawarar yayi aure,Tunda dai bazai iya kara Tunkarar malika ba,gwara ya neman ma kanshi mafita duk da yana tsoron kada Ummi da Abbi su dakatar dashi. Koda ya koma gida,gim da rai yayima malika,yana ijemata takeaway dinta ya Shige daki,ya kulle koda tazo da littafan karatunta taji kofarshi akulle,sai kuma taji jikinta yayi mata sanyi Ranar dukkansu ba wanda yayi barci,shi yana Mukurkusun Ciwon mara da fama da sha'awarta,ita kuma tana juye juyen damuwar da Saleem yake ciki,kwata kwata hankalinta yaki kwanciya,Har da safe ma daya Fito data gaisheshi dakyar ya amsa yana wani cin mgani,Tana so ta sanar dashi Abunda yafaru a asibiti ammh kuma tana jin tsoro,shine da kanshi ya tambayeta,cikin faduwar gaba ta sanar dashi,Harara ya zabgamata yana mata fadan meyasa bata kirasa ta gayamsa ba..? saboda ta rainashi ko? toh in tagaji da zama dashi ne,toh shima ya gaji zai maidata wajen mahaifinta bazai iya karban amanar ba,ta inda yake shiga batanan yake Fita ba,Zuru tayi tana digan hawaye,hakuri takeson bashi,ammh ganin yana cikin zafi shiyasa ta kyaleshi har ya Fice daga gidan yana ta bata rai,shiko aranshi baijin dadin Abunda yake mata,ammh haushin shi daya shine ita tajamai yake kwana yana Fama da tamkewar mara,shiyasa sai ya sauke komai akanta,Kuma Abun takaichi sai yayi mata fada,yakoma yana Fama da damuwa,duk da bazai iya bata hakuri ba,ammh babban Abunda ke dafamai zuciya shine Kukan Malika.,Kukanta na bala'in dagamai hankali barin ma ta kalleshi tana share hawayen,sai yaji jikinsa yayi sanyi kamar ya Rumgumota yayi ta lallashinta,ammh jin kai yahanashi. *Ina godiya sosai da addu'o'inku ga Mama,Allah ya saka muku da alheri....* *Momyn ladingo ce* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _*MALIKA MALIK..,Mallakina ne Halak malak ni Janafty ba mallakin Wani ba,so kudin karatu kuka biya bana Mallaka Ba,ni nake da hakki sarrafa buk dina yadda naga dama,Littafi bazai zama mallakinki a #200 kachal ba,Inhar zakuyi ma kanku Adalci..BAZAN GAJI DA MAIMATA KALMAR KURIKEMIN AMANABA KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*_👏🙏 *19*   ------------------------"Har Weeked din tazagayo Saleem bai sakarma Malika ba,Kullum Fuskarshi ba Fara"a,Karatunta kadai yake kokarin yimata shima ba cikin dadin rai ba,kamar yadda ya saba ba,Shiyasa duk karatun ya Fita akanta,Damuwa tayi mata yawa kuma bata da wanda zata Fadamawa,sai Allah shi kadai take kaima kukanta dayayi mata mganin Abunda ke damunta. Daga wannan Fushin rashin dalilin da Saleem ya hauta dashi Ta fahimci ta fada tarkon sonshi mai tsanani,Domin ta azabtu sosai,ashe koda baya mata mgana sosai,Fuskarshi dayake sakar mata ma kadai Tana sata nishadi,ammh da zarar ya bata rai Shikenan itama zata Shiga damuwa,balle wannan karon da Fushin nashi ya tsauri dayawa ne ta rasa ina zata saka kanta taji dadi.... Yau ta kama Lahadi ne,Tun safe ya Shirya cikin wata dakakkiyar Shadda Navy blue,mai maiko da yarari tana Falo tana gyarawa ya Fito daga dakinshi yana daura agogon hannunshi,da ganin yadda yake komai cikin hanzari zaka Fahimci sauri yake,ganin Fitowarshi yasa ta rankwafa tana gaisheshi akufule ya amsa kafin ya dago kanshi yana kallonta kanta na duke kasa,tana wasa da Kwalliyan hannun Bakar Doguwar rigar dake jikinta. ido ya samata kawai yana kallonta,cike da mamakin ganin yadda tayimai rama ido,Gyara tsayuwa yayi kafin yadan yi gyaran murya yana Fadin"Armm nace ba.."Dagowa tayi cikin tsoro da mamaki tace"Na"am me kace..? Kur yayi mata da manyan idanuwanshi yana wani shafa gemunsa da hannunsa guda,saurin kauda kai tayi jikinta yakama bari haka kurum,yana lura da ita,kawai sai ya barsa yace"Zan yi Doguwar tafiya yau,bansan ya zamuyi da abincinki ba.."Yafada yana kara gyara zaman rigar jikinsa. Kanta na kasa tace"Ba damuwa akwai sauran Fura jiya,kuma maman Abba ta kawomin Faten wake jiya,toh banci ba,sai naci shi yau.."Bai damu ba kawai ya tabe baki ya Wuce yana wasa da makullin motar dake hannunshi yana Fadin"Ok sai na dawo.."Mikewa tayi tana bin bayanshi da kallo cike da sha'awa murya chan kasan makoshi ta Furta"Adawo lafiya Allah ya tsare.."Addu"arta tamai dadi sosai har sai da ya waigo yana kallonta,ita kuma tayi saurin Kauda kai,tana cigaba da kakkabe kujera,Mirmishi yayi yana kallon cikinta wanda ya tasa,kafin ya kada kai ya juya yana Fadin"Nagode da adduanki.."Ya furta cikin muryan kulawa da jin dadi,Kafin ya Fice da sassafa yana takunsa na isa da takama mai cike da jarumta. Sai da ta tabbatar daya Fice kafin ta koma bisa cafet din Falo tayi zaman dirshan hannuwanta dafe da kirji tana dan ware ido kafin ta bude Lebe kamar tana kwakwaiyon mgana ta furta.._Nagode da addu'anki.._……" Tafada tana Wani lumshe ido,kamkame jikinta tayi tana dariyan jin dadi,cikin jikinta tabi da kallo kafin ta kuramai ido tana shafashi take fadin"Boy katayani murna Abbanka ya yafemin laifina,har yayimin mirmishinsa din nan,mai tsada kuma yayimin godiya.."Tafada tana bayyanar da jin dadinta,ganin babu mai bata amsa yasa ta rarrafa tatashi ta cigaba da Abunda takeyi,ammh ranta fes,gefe daya kuma yau Saleem din yafi koyaushe yimata kyau,don ta yaba da wankan sosai,sai kuma ta Fahimci cewa kamar in yasa manya kaya yafimasa kyau sosai,barin ma ya karya hulan nan nasa,wayyo kamar taje ta Rumgumeshi ta lasan mai baki haka takeji. __________________ Sai da ya Shiga cikin kano kana ya kira Zahra ya fadamata gashi a kano,kinga zahra kamar kanta zai Fado kasa saboda zumudi,dama already Tun jiya da sukayi waya ya sanar da ita yau din yana tafe,so Tun safe gidan ya rikice da hidiman taron bakon Zahra,wacce takejin kamar ta bude ido ta ganta agaban Saleem. Hajiya saratu wacce suke kira Momi itama Zahra har mamaki take bata ganin barin jikin Datakeyi,har sai da tayimata fadan saura in saurayin yazo karta kama kanta Tunda ta riga tasan halin kayanta,Mirmishi kawai Zahra tayi aranta tana Fadin"Momi bata san so ba.."Koda Saleem ya kira Yace gashi ya shigo kano sun riga sun kamallah komai har zahra ta buga wanka da kwalliya cikin wata dakakkiyar Shadda mai ruwan orange,ammh light dinta dinkin Riga da zani ne,Tayi daurin ta wanda ya Fitar da gashinta wanda ta daureshi da band daga baya,Fuskarta cikin Simple make up,wanda Nadira ta bata lokacinta wajen tsansara mata ita,abinci ko basu san adadin kala nawa suka girkamai ba,balle ababen sha da suma babu kalan wanda ba"ayimai ba,ga kuma surkin irin na kwali ma"ana na bature Kai tsaye Zahra ta sanar dashi ya tambayi Anguwan GRA,in yazonan ya Tambayi gidan tsohon alkalin alkalai Bukar mada,za"a nuna masa,haka ko akayi dayake gidan ba batattace bane,bai sha wahala ba,sai gashi ya faka motarshi kirar 4matic acikin kayatattacen haraban gidansu zahra,Koda ya Fito daga motan ya hankalce yake bin gidan da kallo yana Dan tabe baki,Megadi ne ya kariso da hanzari ya rankwafa yana gaisheshi ya amsa daidai yana kiran zahra,sanda ta Dauki wayan yake sanar da ita gashi aharaban Gidansu ta Fito. Tsalle ta buga tana dafe kirji bakinta yaki Rifuwa,zaman mayafin jikinta Nadira ta gyara mata tana kara Fesa mata Turare take Fadin"Oy act very well best,nasanki banda rawan jikin nan,naki da kuma shegen kanki dabaya zama waje daya."Tafada tana dunguremata kai,dariya tayi tana Ficewa cikin wani taku,kafarta sanye cikin wani ubansu takalmi mai dan Tudu ammh ba sosai.. Afalo ta tarar da Momi zaune cikin yauki da Murna tace"Momi ya iso fa..",Da kallo ta bita kafin ta mike tana Fadin"Masha Allah,ki mishi sannu da zuwa,Ammh don Allah ki natsu Kinji zahra..",Tana yar dariya ta Rufe Fuska tana fadin"To momi.."Tafada tana wucewa zuwa kofar da zata sadata da haraban gidan. Tundaga nesa ta hangeshi yana jingine jikin motarshi yana latsa wayarsa,takowa take gareshi cikin wani taku,kamar wata hawainiya,ammh duka idanuwanta na kanshi harta kariso gabanshi bai sani ba,sai da yaji wani Sihirtattacen kamshi ya dukeshi kana ya dago suka hada ido da ita,Ajiyar zuciya ya sauke ya maida wayarsa aljihu yake Fadin",Madam sai yanzu,? bayan kingama shanyani awaje..? Wani mirmishin dariya tayi tana kulle idanuwanta da tafukan hannunta take Fadin",Am srry,Barka da zuwa jahar kano,koda mai kazo an Fika..."Dan mirmishin yake yayi yana binta da kallo afaikace kafin yace"Au! haba..?Ashema hakane.."Yafada cike da dan barkwanci,dariya tayi mai sauti kafin ta juya tana Fadin",Yanzu dai duk ba wannan ba,mu shiga Daga ciki.."Bai yi gardama ya fara binta abaya ita ko jin kamar yana kallonta,sai yasa salon tafiyar da Nadira tagama koyamata duk sai ta rude ta fara hardewa kamar zata fadi. Shiko Saleem idonshi kur akanta cikin mintina ya kare mata kallo,Mele baki yayi aranshi yana ayyana Malika ta Fita komai na cika amace,ammh kuma duk da hakan zai iya maneji,ammh Shegen rawan kanta ne ke bashi haushi,domin ta gwadamai har suka isa falon bakin ta nuna mai daya Daga ciikin kujerun Falon,ya samu waje ya zauna yana binta da kallo,ciki ta koma sai kuma chan ta dawao tazo ta zauna akasa suna kara gaisawa tana tambayanshi ya mutan gidan. Basu jima ba sai ga Nadira da yar aikinsu sushigo da manyan Farantai shake da kololin abinci,daya kuma shake da jugs na Lemukan da suka hadamai,Nadira ta zauna suka gaisa sosai harda dan barkwaci yayi mata,kusan dai mutumin naku shima in yaso wasa toh babu wanda yakaishi iya barkwanci da Raha. Fita tayi ta basu waje suka cigaba da hiransu,wanda duk rabin hiran Zahra keyi,shiko sai jefi jefi zaiyi dan dogon mgana,ammh daga gyada kai sai mirmishi in yazama Dole,ada bai yi niyyar cin komai ba,ammh zahra ta nuna bataji dadi ba harda hawayen karya tayimai,shiyasa yace ta sanyamai Sinasir,da miyar ganye,wanda yaji manshanu da naman Rago yaji kuma dayawa saboda Dama sinasir mutuminshi ne,shi da waina yana sonsu sosai. Lemun kuma kunun ayan yasha sosai,sai zobon shima dai baisha da yawa ba,sun sha Fira har anan yake sanar da Zahra cewa Basu rabu Da malika ba,kamar yadda Duniya ta dauka,so yanzu hakama tana zamfara tare dashi ya sanar da ita  hakane saboda yana ganin kila yayi maneji da ita,Sanda ya sanar da ita taji ba dadi ammh soyayyarshi ta Rufemata ido,ta sanar dashi babu komai,ko da'ace Itace ta hudu tana sonshi ahaka kuma zata aureshi yaji dadin mganarta ya sanar da ita da zarar ya koma gida sai Tuntubi mahaifinshi yadda suka yanke zai sanar da ita ta waya,Ai murna kamar Zahra ta Shide,sai kace ance gobe ne bikin. Sai After 4 kana yayi Shirin tafiya,bai Tafi ba sai da zahra ta shiga dashi babban Falon gidan ya gaisa da momi,wacce ta yaba dashi sosai Fiye da Tunaninta,domin bata zata cewa zaben na zahra ya Wuce tsara ba haka gashi kuma dan manyan gida ne,cikin Fara"a da kunyar Diyar Fari ta amahesu suka gaisa kafin yayi musu sallama Su Zahra da Nadira suka rakosa har wajen mota,suna karayin sallama kenan sukaji hon,megadi ya bude get,sai ga wata bakar motar BUGATTI,Ta sawo kai cikin gidan,kusa da motar Saleem aka faka motar kafin direban ya Fito da gudu ya bude bangaren baya Alkali bukar mada ya Fito yana gyara zaman babban Rigan jikinsa. Zahra ce tace"La..Shikenan ma Nadira ga Abba nan.."Tafada cike da murna,shiko saleem gabanshi ne yafadi,gaakiya bai so sukayi arba ba,ganinsu tsaye yasa ya kariso yana kallon Saleem cike da mamaki,Tunkafin yayi mgana Saleem ya rankwafa yana gaisheshi,hannu ya bashi suka y musabaha yana kallon su Zahra tun kafin yayi mgana Nadira tayi karaf tace"Yauwa Abba gwara daka dawo,Saurayin Zahra ne yazo ACP SALEEM KABIR KUMO.." Abbah yace"Masha Allah,.."Yana mirmishi yana kuma kallon Saleem,Zahra ko Fuska ta Rufe tana juyar dakai,Yar dariya Abbah yayi yana Fadin"Hakane..? to ku koma gida zan yi mgana dashi.."Nadira ce tace"To Abba ashigo lafiya.."tafada tana jan hannun Zahra wacce ke dagama Saleem hannu afakaice,sai da suka shige kana Abbah ya dawo da kallonsa kan Saleem yana Fadin"Sannu da zuwa.."Kan Saleem na kasa yace"Yauwa Abba,mun sameku lafiya.."Ya karba da lafiya lau.,daga ina kake,ma"ana waye mahaifinka.." Bai yi gardama ba ya Sanar dashi sunan mahaifinshi,cikin jin dadi Abba yace"Masha Allah,tafiya tazo da sauki,ai Mahaifinka ba boyayye Bane,ikon Allah,munsan juna chan abaya gaskiya,kodai mene zan tabosa ta waya insha Allahu.."Yafada yana bayyana murnansa Afili,Saleem yayi kasake yana jin Bukar mada na Shirin ballo masa ruwa,Abbi da baisan da wata mgana ba,yanzu in ya samu lbrin mai zai ce mai..? Shiyasa har sukayi sallama ba cikin dalin rai ba,Wani karin fargaban ma,shi da kanshi ya umarceshi daya bashi nombar Abbi,kuma ya sakamai yana jin cewa yagama yawo,Abunda yafi bashi tsoro shine har yana sanar dashi ya kwantar da hankalinsa kamar ya samu zahra yagama. Har yakai zamfara yana Tunanin irin matakin da Abbi zai dauka akanshi in yaji lbrin yana neman wani auren batare da saninshi ba,bai shiga gida ba sai da ya biya yyima Malika takeway,koda ya koma gidan bayan sallar mangari ne,Ta idar da sallah kenan ya Shigo,bai jira ma tayi mgana ba,bayan amsa sallaman datayi ya ijiyemata lodojin daya Shigo dasu ya Fice zuwa dakinsa yana jin jikinsa agajiye kamar wanda akayima mugun Duka,yana shiga dakinsa ya Tube ya Fada wanka yana jin Barci yana Lumshe mai Ido. Abunda Saleem yake gudu shi ya Faru,don bayan dawowarshi gidansu Zahra da kwana biyu yana office da rana tsaka ya samu kiran Abbi,wanda sai da gabanshi ya Fadi,ya daga yana mai sallama Abbi sai ya karba sallaman kafin ya zarce da Fadin"Ashe kuma aure kake nema bamu da lbri...?"Wani yam yaji,kunya da tsoro duk sun kamashi,Sosa kai yafarayi kafin yace"Injiwa Abbi.."? Ya dakatar dashi da Fadin"Inji uban yarinya,jiya da yammah Tsohon Alkalin Alkalai ya kirani Bukar mada,ya sanar dani cewa kun ma daidaita kanku kaida yar wajensa,daga karshe ya jadaddamain ya baka Auren yarshi Duniya da lahira.." Wani zufane ke ketomai ko tako"ina Dakyar ya samu zarafin Cewa"Tsaya kaji Abbi,wlh sau daya na..."Yimin Shuru mallam ba wannan na Tambayeka tunda kanunama Duniya bamu da daraja awajenka Saleem ai Shikenan,da ka boyemana ni ko Aisha akwai wanda ya isa ya hana ka kara aure ne? wlh babu saboda haka na kira ne na sanar dakai Sati mai kamaawa zan kira kumo,Baffa zai zo mu tafi kano ane ma maka aurenta..."Daga haka ya yanke kiran. Tsaye saleem ya mike yana Goya hannunshi abaya,gashi da Abunda ke ranshi ne,kuma wanda yake bukata Abbi ya sanar dashi,ammh yaki farinciki baisan dalili ba,baya Farinciki da Auren Zahra kwata kwata arayuwarshi ga kuma Abbi ya dau Fushi dashi,ganin bashi da mafita ne ya kwashi rawan jikin kira ya marwan yana sanar dashi Abunda ke Faruwa,baki ya rike yana Mamakin me Saleem zai zama age dinshi yaron da ko 30 bai gama cikawa ba,Har zai ijiye mata biyu da ya jefamai tambayan ina zai kai mata biyu..? Kasa bashi amsa yayi don bazai iya sanar dashi rataye Malika yayi ba Shiyasa yake son kara aure,shidai rokon shi daya Ya kira Abbi da Ummi yabasu hakuri ya sanar dasu abunda yafaru,ganin ya damu ne shiyasa ya lallasheshi da cewa yanzu zai kira Abbin suyi mgana. Koda Marwan ya kira Abbi,bayan sun gaisa yake sanar dashi Abunda Saleem ya gayamai,Mirmishinsu na manya Abbi yayi kafin yace"Rabu dashi Marwan,Yarinta da Shirme na damun kaninka,Nayi alqawarin bayan na shiga mganar auren nan daya dauko zan zare hannuna a sha"anin Rayuwar Saleem,saboda naga kamar ni na zama mai Takura gareshi.."Jin haka yasa Ya Marwan ya dinga ba Abbi baki,ammh yace shifa ya riga ya rantse so kawai yama barma mganar,dole ya hakura domin yafi kowa sanin Abbi kaifi daya ne. Mganar da Abbi ya sanar dashi ya tabbata domin Ranar sati,da daddare bayan sungama karatu da malika sai ga wayar Zahra,nan take sanar dashi dazu su Abbinshi suka bar gidansu,kuma ma wani karin albishir an sanya musu ranar aure wata biyu masu zuwa,mganar tazomai abazata,haka yayi tagumi rike da waya yana jin zahra kamar ya fashe da kuka,Zuciyarsa bata karkata da Abbi ko Ummi, ba tafi karkata ga Malika tana tambayanshi anya ko yayi mata adalci Abunda yake Shirin aikatawa,duba da Halin data ke ciki,cikinta ya Fito sosai dayake tana da girman ciki,yanzu kawai ya sanar da ita zai kara aure ya zataji.."? Kawai zuciyarsa takasa natsuwa waje daya,duk sai yaji Danasanin biyema Zahra ma dayayi balle har yaje gidansu. Zuciyarsa taki bashi karfin gwiwan sanar da Malika Abunda ke Faruwa,sai kawai ya share zuwa gaba ya sanar da ita,Sati daya da saka Ranar Ummi ta kirata da yammah,ranar ko ta koma awo,tadawo agajiya tana kwance kan kujera tana maida Numfashi,Bayan sun gaisa Ta tambayeta jikinta ne,tace mata da sauki yanzu tadawo daga asibiti,sai Ummi ta fara mata Nasiha da zaman hakuri kafin ta gangaro tana sanar da ita sai ta kauda ido game da Saleem da sabuwar amaryanshi duk da batasan ina zai ijeta ba.." Tana kwance ne sai da ta zabura ta mike zaune tana Dafe kirji cikin Fitan hayyaci,Tama kasa cema Ummi komai kawai idanuwantane suka ciko da kwallah tana girmama girman tsanar da Saleem yayimata,ashe duk hasashen datakeyi gaskiya ne ya rataye tane saboda amanar mahaifinta bawai don shi yana Ra"ayin zama da ita ba,gashi zai auro wacce yakeso su zauna tare,ita kuma ko oho,Bayan sungama waya da Ummi takasa zama waje daya,zuciyarta na mata zafi,dan cikinta sai motsi yake,nan ta zube bisa Cafet din Falo tana ta kukan tsausayin kanta,batason haka take mugun son Saleem ba sai yau da akace zai yi aure,ji take kamar ta kashe kanta saboda bakinciki,ta riga tasani ita tazama bora shara,dama yaya lafiyar kura balle tayi zawo. Haka yazo ya sameta cikin wannan Halin,daya tambayeta meke damunta,kawai sai tace cikinta ke ciwo,ya damu ya duka kusa da ita yana kallon cikin yake tambayanta ko su tafi asibiti ne? Kai ta girgizamai kafin tacemai ita ta sha mgani zai bari,Ganin yadda take kallonshi asace tana sharan kwallah ne zuciyarsa ta fara zargin wani abu,Daga karshe ma rarrafawa tayi ta mike ta shige dakinta tana Sharbe hawaye,da kallon mamaki ya bita,domin ranar ma ko takeawy din dayayimata ma bata kallah ba,balle har yasa ran zata ci,Dayakoma daki yayi ta tunanin kodai wani ya sanar da ita Abunda ke Faruwa ne,ammh kuma baya Tunanin haka,Saleema ce mai bakin rariya kuma basa shiri,ko shi din ma ya rage sakarmata Fuska don ya gane tana da raini ne,ganin bashi da amsa tambayoyinshi yasa ya watsar da batun ya cigaba da harkokinshi ammh bawai don bai damu ba,A"a sai don yana wofantar da Abun karya bashi muhimmanci. Ko washegari da zai Fita sai da ya lekata tana kwance cikin bargo idanuwanta sun kumbura saboda kuka,Domin kwana tayu tana kukan tsausayin kanta da kishin Saleem daya hanata Runtswa,sai ajiya takara sanin cewa soyayyar Saleem yayi mata mugun kamu sosai,domin kishinshi ya kusa illata jiya,ga yunwa taki cin abinci.ganinta cikin wannan halin ya bashu tsoro har Saida ya zauna gefen gadon,yana yaye bargon data Rufa dashi,hannunta ya riko yaji zafi sosai,har saida ya dago yana kallonta kanta na bisa Filo tana kallonshi itama cikin wani yanayi. Kuri yayi mata da ido,yana kallonta kafin yace"ke wai meyasa kin cika Taurin kai ne *MALIKA..*.."Yafada cikin wani yanayi yadda yakira sunan nata,sai da tajishi har tsakiyar kanta,Lumshe ido tayi tana jin wani yarr,balle ma yadda yaketa murza tafib hannunta,Cigaba da cewa yayi"Tun jiya nace miki ko zamu tafi asibiti ne kika ki yarda wai kinsha mgani,don Allah kalli idanuwanki yadda suka kumbura suka chanza kala?ko haka kikeso na barki daga baya wani abu yafaru Abbi da Ummi ko Daddynki suce da gangan  naci amanarki ko..? Dakyar ta iya bude idanuwanta cike da kwallah tace"Bafa wani abu bane,nama ji sauki.."Tafada tana kauda kai,Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya mike bayan ya saki hannunta,wanda shi kanshi Taushin hannun nata yafara dibamshi zuwa wani yanayi na dabam,A kaikace yace"Toh naji kin samu sauki,yanzu dai kya bari ko Maman Abba nama mgana tashigo ta dubaki kafin tatafi asibiti..",Jin ya ambaci Maman Abba da hanzari ta dagamai kai,tana share kwallah,Ido ya sakamata har ya kada kai zai Fita ya dawo da baya yana Fadin",Wai don Allah na tambayeki mana? wannan Koke koken duk miye silanshi,da nayi miki mgana daga jiya zuwa yau sai ki kama min kuka kina Share min kwallah,Nayi miki wani abu ne Daya bata miki rai..?"Yafada yana mai kureta da ido,duka hannunsa Sarke cikin aljihun wandonsa,na american Suit dinsa. Runtse ido tayi tana Kyabe baki tace"Allah ba komai.."Ta fada tana juya baya,kada yaga hawayenta,Ya dade yana kallonta kafin ya kada kai yafice Abun na mishi ciwo,ace yarinya bata da aiki sai kuka,haba ai abun yayi sosai,gashi kukanta damunshi yake,in yana kaunar mutuwarshi toh yana kaunar kukan Malika,ita kuma bata ganewa Yayi sa"a yana Fita yacikaro da Baban Abbah zai Tafi kai danshi mkranta Daga chan ya Wuce wajen aiki,wajensa ya karisa suka gaisa kafin ya tambayeshi ko Maman Abba na nan,don Allah yana so ta shiga ciki ta duba mai dakinsa ce,batajin dadi,Baban Abba da kanshi yakoma cikin gida ya sanar da Maman Abba sakon Saleem batayi jinkiri ba ta sanyi hijabinta suka Fito tare,nan suka gaisa da Saleem din yace zai Wuce in akwai wata mtsalane su nemasa awaya,Adawo lafiya tayi mai kafin ta Shiga gidan Aranta tana Fadin"Insha Allahu ma ba mtsala"Sukuma magidanta kowanne ya Shige motarshi zuwa wajen aiki. Halin Da Maman Abba taga Malika ya bata tsoro,da hanzari ta dagota daga kwancen tana Fadin"Madam meya sameki haka? jikinki ya dau zafi,Allah yasa ba maleria bace ke son kamaki ba..,? Rau rau Malika tayi da ido kafin tace"Bansani ba,kilama itace..."Tafada wasu hawaye masu zafi na zubomata,Kuri Maman Abba tayi mata da ido kafin tace"Kinga idonki kuwa? kuka kisha haka,alhalin kisan irinku ba"a son suna shiga damuwa ko zama da ciwo haka.."Jin haka yasa kuka ya ciyo Malika batasan sadda ta fada jikin maman Abba tana Fadin"Toh ya zanyi..? Maman Abba ki Fadamin ya zanyi? Aure zai fa zai kara.."Tafada cikin gunjin kuka tana Rumgume maman Abbah. Maman Abba datayi mutuwar zaune jin Statement din Malika na karshe da azama ta dagota hannuwanta dafe bisa kirjinta tace"Ki!...Me?Kishiya fa kikace? wai da gaske kike Madam..?Malika na kuka tace"Wlh da gaske nake,kuma bai sanar dani ba mahaifiyarshi ne, ta kirani take gayamin.."Zaro ido Maman Abba tayi kafin tace"Ke don Allah..? Kina nufin shi bai sanar dake ba? kan durun jar uba ni Samiha,Yo Allah na tuba ni kishiya ko tashiga motar hayace ai bana bukata,balle ta raba miji.."Tafada tana jinjina Abun. Kan kafadarta Malika ta yada kai tana kuka,Rumgumota Maman Abba tayi kafin tace"Ammh ko bai kyauta ba,ai ko bakomai kyaci darajan cikin dake jikinki da kuma soyayyar data hadaku zuwa ga aure.."Dagowa malika tayi tana kallon Maman Abba kafin tayi mata mirmishin yake tace"Bazan ci wannan darajan ba Maman Abba,ba auren soyayyah mukayi ba,hasalima auren mu ba kan Turban zama bane,an kulla shine kan Turban _SAI NA RAMA_………" Jagale Maman Abba tayi tana kallonta kafin tace"Ban fahimceki ba..."Tafada cike da mamaki,gyara zama Malika tayi tana kallonta kafin tace"Nasan bazaki gane ba,sai kinji lbrinmu daga Farko har karshe..."Nan Malika ta Shiga bama Maman Abba tarihin rayuwarta Tundaga farko har zuwa aurenta da Saleem,da komai da komai bata iya boyemata ba,ta karishe tana Fadin"Na sanar dake lbrina ne,Maman Abbah domin kila kina da hanyar da zaki Taimakamin,wlh inason Saleem so mai tsanani,ammh naga alaman ni bana gabanshi ya tsaneni,Tun kuskuren dana aikata abaya,ya zanyi..? Wani mataki zan dauka nima yasoni kamar yadda mazaje keson sauran matansu..? Tafada tana tsananta kukanta,Sai gashi Maman Abba ma kuka take,kukan tsausayi Malika da kuma rayuwar datake ciki,Riko tayi ta mikar da ita tsaye tana Share mata kwallah tace"Hakika lbrin rayuwarki Abun tsausayi ne Malika,ki kwantar da hankalinki insha Allahu sai inda na gaza,zan taimaka miki wajen samun soyayyar mijinki ahannunki,wanda nake da tabbatacin cewa shima yana Sonki.."Malika ta girgiza kai tana Fadin"Bar gayamin haka saboda naji dadi ni nasan cewa Saleem bayasona ya tsaneni.." Maman Abba tace injiwa? wlh dabaya sonki babu wanda zai tilasta mishi   zama  dake Malika,yana sonki buh Shikanshi baisan yana sonki ba,kece ya kamata kitafiyar dashi ta hanyar da zai bayyanar da son nashi batare daya sani ba.."Zuru malika tayi mata kafin tace"Ta yaya kenan..? Mirmishi Maman Abba Tayi kafin tace"matso da kunnanki kusa kiji.."Da hanzari malika ta matso da kunnanta Maman Abba tayi mata rada,wanda ya sata sakin mirmish,gira maman Abba ta dagamata tana Fadin"To ya..? Mirmishi ta saki kafin ta bata hannu suka Tafa tana Fadin"Mu wayewar banza ai muna da ita Maman Abba,barikin ce kadai bamu kware akai ba.."Dariya suka sheke dashi kamar basu bane dazu suke kuka ba. Maman Abba bata tafi ba,sai Da rana ta kana ta koma gidanta tayi aiki ta dora girki,Tunda yau Dutynt dare take dashi,Malika taji dadin shawarwarin Maman Abba,ko banza ta samu mai bata shawara da kuma wanda zata kallah yau amtsayin wacce suke da kyakyawan alaqa da ita,Shikenan jiki ya warware dama kishi ne da rashin abokin shawara,koda Saleem yadawo da rana ya kawo mata abinci ya ganta ta samu sauki,har Fuskarshi taga jin dadinshi ba kamar yadda ya fita da safe ba Ita da kanta ta kira Hajiya binta take sanar da ita auren da Saleem zai yi,Hajiya tayi Shuru aranta tana salallamin Malika da kishiya ai sai Allah,toh meta sani banda gata da sangarta,Hakuri dai tayi ta bata da kuma kara jadaddamata data kula da kanta da Abunda ke cikinta,daga karshe tasanar da ita da zarar Joda ta kamallah Semester ta karshe zata turo mata ita ta taimakamata har ta haihu,Malika taji dadi sosai har sai da Ta nunama Hajiya murnanta tana ta mata godiya. Hajiya binta batayi karambanin sanar da Daddyn Malika Ba,saboda gudun tashin hankalinshi balle akwanakin nan Ciwon nashi yatashi har suna Tunanin komawa ma asibiti asake dubashi,ko tashin jikin nasa ma Shi yace kar asanar da Malika saboda kar hankalinta yatashi har yataba lafiyan Abunda ke cikinta.. ---------------------------- Bayan kwana biyu da yin haka Kawai yana zaune a cikin office dinshi misalin karfe Uku na rana sai ga wayar Abbi,gabanshi har yafadi daya ga kiran,cikin sanyi jiki ya daga kiran,Yana ma Abbi sallama bai amsa mai ba yace cikin wata murya mara Dadi.."Saleem don Allah komai kake yanzu ka bari kataho katsina,asibitin da"aka kwantar da Mahaifin malika zaka zo,domin nima da safe matarshi tamin waya akan nazo jikinsa ya tashi Tub jiya da daddare,basu kwana agida ba sai asibiti,kuma yana ta kiran sunanyeku kaida Malika.." . Zumbur ya mike yana Fadin"Innalillahi...Ganin nan zuwa yanzu insha Allahu.."Yafada yana goge zufan dake kwararo mai ta saman kanshi,bai dauki komai ba,sai makullin motarshi ya Fice da hanzari yana addu"an Allah ya tashi kafadan Daddy ko gida bai koma ba,daganan ya dauki hanyar katsina bai ma Tuna daya biya ya sanar Da malika ga inda zashi ba,jin yanayin muryar Abbi dayaji shi ya tabbatarmai da Jikin Daddyn ba dadi... *Shakira.."* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *20*   Gudu yayi ta shararawa bisa kwalta cikin lokaci sai gashi ya isa cikin asibitin da misalin karfe 5:30Pm na yamma,koda yaje ya tarar da Abbi da su hajiya binta da wasu yan"uwanshi dake Malumfashi dukkansu awaje abakin Emargency suna ta koke koke,Hankalinsa tashe ya karisa wajen Abbi yana rankwafawa ya gaisheshi. Dagosa Abbi yayi idanuwansa sun chanza launi yana Fadin"Ina malika? meyasa baka taho da ita ba,?tana bukatar ganawa da mahaifinta..",Jikinsa asanyaye yace",Wlh Abbi daga office nake ko gida ban koma ba,na kamo hanya,ammh zuwa gobe sai naje na taho da ita.."Bai samu zarafin mgana ba wani likita ya Fito daga cikin emargency din hankalinshi atashe yake Fadin"Wai Saleem din ya kariso..? Da hanzari Abbi ya riko hannunshi suka nufi Dr yana Fadin"Allah ya kawo shi Dr,.."Bai yi mgana ba illah kallonsu da yayi yana Fadin"Ku biyu kadai na yarjema ku shiga,kuma don Allah minti biyar plz,kuduba halin dayake ciki.."Gyada mai kai Abbi yayi,shiko Saleem Tuni ya tura kai cikin dakin hankalinsa a matukar tashe. Hajiya binta ta kariso tana hawaye Tun kafin tayi mgana liktan ya dakatar da ita da hannu yana Fadin"Don Allah hajiya ki koma baya,ko baki ga halin da yallabai yake ciki bane,Kuna fa ciki tun dazu kuna koke koke,kuma Numfashinsa baya tafiya sai da taimakon oxygen,so don Allah go back,ku barmu muyi aikin miu plz.."Ya fada yana hada hannunwanshi kafin ya juya ya Wuce cikin sassarfa,da kuka hajiya takoma baya tana Rufe hannunta da Hijabin jikinta. Saleem bai san yadda hawaye yake Fitowa daga idanuwan Namiji ba,sai yau domin lokacin daya karisa gaban Gadon Daddy bai iya ganeshi ba,ganin yadda gabadaya halittanshi ta chanza Fuskarshi da bakinshi sun zaganye babu kyan gani,Numfashinsa baya tafiya sai da taimakon oxygen,Gashi dai yana kallonka,ammh kuma sai dai kaga yana zubar hawaye kawai,durkuso yayi agaban gadon yana riko hannun Daddy mai lafiya,lokaci daya yaji hawaye mai Dimi sun zubomai.. Daddy daya ga Saleem ne rike da hanunshi,sai yafara so yayi mgana ammh babu hali,sai mika hannu yake yana zaburar jiki,Kai tsaye saleem yasaka hannu ya ciremai Oxygen din yana Fadin"Daddy gani nan,nine Saleem.."Bakin da Daddy akarkace yana zubda miyau yake Fadin"Ina...Ina malika..? Cikin dabar dabar da bakowa zai gane ba,Saleem na goge kwallah yace",Tana zamfara Daddy tafiyan agaucene shiyasa ban zo da ita ba,ammh gobe zan je nazo da ita insha Allahu.." Shuru Daddy yayi yana maida Numfashi kafin ya damko hannun Saleem gam yana Fadin"A"a kabarta baisai tazo ba,bana so tazo taganni cikin wannan halin,nafison ta ga gawata Fiye da ganina cikin halin jinya,Amanar dana baka zan kara jadaddama,Saleem don Allah ga Amanar malika nan da Dukiyarta kaine gatanta yanzu bata da kowa,don Allah karka barta kada ka gujeta balle kaba Rauninta damar illata rayuwarta.."Yafada yana maida Numfashi sama sama. Mikewa Saleem yayi agaugauce yana Fadin"Haba Abbi,wai bazakayi mgana afitar da Daddy waje ba,Tunda sunkasa komai.."Yafada cikin Fita hayyaci idanuwansa sun chanza kala,Kinsakin hannunshi Daddy yayi yana girgiza kai yace"Karku damu dani,ni tawa ta kare,Nidai Fatana don Allah kada kubarmin malika cikin kunci don Allah,ku kula da ita,ka rike mata Dukiyarta kar ka bata har sai ta kara mallakan hankalin kanta..Da..da.ga...Kar...She...ina son Ku..Sanar...Da..ita...Na yafemata..Nima...Ta..yafe...Min...."Yafada Kirjinsa na wani tasowa,Yana shirin Shidewa,Da hanzari Saleem ya kwasa gudu zuwa waje,shiko Abbi hanzarin daukan Oxygen din yayi zai mayar mai, Daddy ya kauda kai yana Fadin"Ka..Bar..Ni..Na..Cika...Da..Kal..mar..Shahada..Laila... ha'illalahu..Muhammadan Rasulillahi..."daga nan ya kafe idonshi nayin sama,Abbi da jikinsa ke rawa agabanshi aka zare ran Daddy,Hannu ya sanya ya karisa rufemai ido yana kareshe "Salallahu alaihi wasallam.."Yake Fada yana share kwallah,daidai lokacin da Saleem ya shigo da zugan likitoci. Turus yayi yana kallon Abbi dayake Hawaye,Baya yafara ja yana Dafe kanshi,da hanzari likitocin suka karisa ga Daddy suna gwaje gwajensu,basu dau wani lokaci ba,suka ja mayafi suka Rufeshi kafin su waigo suna kallon Abbi,kai Dr ya girgizamai kafin yace",Am srry We list him.."Yafada kafin ya kada kai ya Fice daga dakin da hanzari sauran ma suka Rufamai baya. Kukan zucci Saleem keyi,domin na sararin yaki zuwa,Wani imani na kara Shiganshi,Malika yake Tunawa yana tsausayin halin da zata Shiga in taji lbrin rasuwar gatanta Aduniya,Abbi ne yazo ya rikoshi yana bashi baki suka Fita waje,ganin halin da suka Fiti ya sanya su hajiya ta tabbatar da zarginsu kan Daddy,Kanta ta tusa cikib hijabi tana kiran sunan Allah,,Suko yan malumfashi hannu suka dora akai suna kuka tare da Fadin sun bani sun lalace. Koda Karfe 7 na dare yayi Tuni har sungama wani cike ciken takarda an basu gawanshi cikin ambulance suka nufo gida dashi zukata cike da alhini da rauni,wanda kafin isowarsu gidan har mutanen malumfashi har sun kariso sun cika gida suna ta keko koke,Lbrin rasuwar Alhaji Abdulmalik Dankasuwa tagama zagaya duka kafafen yada lbrai,sakamakon shi mai jama'a ne,da kuma abokan kasuwancinsa da suke son samun jana'izarsa sai aka sanya Lokacin jana'izarsa karfe ,11am na safiyar Gobe. Abbi da kanshi ya kira Ummi ya sanar da ita rasuwar,salati tayi tayi tana karajin tsausayin malika aranta,nan yake sanar da ita anan zai kwana,saboda haka gobe su taho ita da hajiya,Saleem ko bai zauna ba yayima Abbi sallama akan zai koma yaje ya taho da Malika gobe da safe zasuyi sammakon tahowa,Gyada kai Abbi yayi kafin yayimai Fatan Allah ya kaishi lafiya. Yana Tafiya bisa hanyar komawa zamfara,ammh kukan zucci yake,kukan tsausayi da wani  Shauki da baisan daga ina yake zuwa ba game da malika,Bayason ya kasance shi zai sanar da ita,wannan babban rashin datayi,Ga kuma wani karin Nauyin Daya rataya awuyanshi na girman Amanar dukiyar Malika da Daddy ya bashi kafin ya cika,hakika Daddy ya cika mumunin kwarai,Allah ya karbi bakuncinsa Ameen. Sai karfe 11:08pm na dare ya saka motarshi acikin gidan bayan yayi hon megadi ya budemai get,Koda ya faka motar a parking space,kasa fitowa yayi saboda yadda ko"ina na jikinsa yayi sanyi,agogon dake daure ahannunshi ya duba,kafin ya kada kai ya Fito yana amsa gaisuwan da megadi ke jeramai bai jira cewarsa ba ya nufi cikin gidan cike da fargaban da wani ido zai kalli Malika yace mata babu Daddy yau yatafi ya barta... Yana saka kanshi cikin Falon yaci karo da ita zaune kan kujera tayi tagumi da hannun bibbiyu,tana ganinshi tayi saurin mikewa tana raba ido,da alamun bata cikin natsuwarta,Shiko tsaye yayi yana kallonta yana Fitar da Numfashi sama sama,Ganinta kaawai sai ta kara sanya jinin jikinsa yayi gudu,Kuramai ido tayi tana karantar halin dayake ciki,cikin son nuna jarumta yafara taku zuwa gareta yana kara Kankance idonshi don karta fahimci halin daya ke ciki,itako Tuni ta fahimci Something is wrong. Sai da yazo gabanta kafin ya zura hannunayenshi cikin aljihun wandonshi yana kallonta kai tsaye yace"Me kikeyi har tsawon wannan lokacin baki kwanta ba.."? Rau rau tayi da ido tana kallonshi kafin tace"Nakasa barci ne wlh,gabadaya zuciyata babu dadi gabana keta faduwa,tunda dazu da mangariba,kuma na kira wayar Daddy akashe,ta hajiya kuma ba'a dauka.Shine..Shine..Gabadaya na kasa natsuwa.."Tafada cikin karyayyiyar murya hawaye na taruwa a idanuwanta Gabansa ne ya fadi da sauri yace"Toh kuma shine Abun kuka,kila network ne yasa baki samu wayar Daddyba,ita kuma hajiya may be bata kusa ne,in tazo taga kiran zata kiraki.."Ya fada cikin karfin hali,ammh baya kallonta kanshi na kallon gefe cike da tsausayinta. Komawa tayi ta zauna bisa kujera tana Fadin",Toh ammh tun dazu haryanzu fa bata kira ba Mallam.."Tafada hawayen datake rikewa suka zubomata,kallonta yayi yana tsausayama Rauninta,Bata bashi damar mgana ba tace"Kuma ni zuciyata namin rawa duk sadda na tuna da Daddyna,ina tsoron ko wani abu ne mara kyau ke faruwa dashi,don Allah Mallam ka gwada kiranta agani ko zata daga.."Jin Abunda tace ne yasa yace"ok bani wayar taki na dauki nombar.."Da hanzari ta mikamai  bayan ta lalubomai nombar hajiyan,bai mata mgana ba, kawai ya Fito da wayarsa kamar yana dauka nomba,nan ko da wayau wayar malika yayima Shoutdown cuz bayason wani ya kirata ya sanar da ita kai tsaye baisan wani hali zata shiga ba. Kara wayar akunne yayi kamar yana kira kafin ya saki ajiyar zuciya yana Fadin"batama shiga ba kwata kwata.."Yafada yana tura wayarsa aljihu harda wayar Malika,Zuru tayimai da ido tana sharan kwallah,ganin haka yasa ya mika mata hannu yana Fadin"To kuma miye Abun kuka anan..? keda kuka bai miki wahala,oy taso kizo kiji wata mgana.."Yafada yana sakarmata idanuwanshi,Kallonsa tayi kafin ta mikamai hannu ya mikar da ita kai tsaye ya jawota zuwa jikinsa,dukkansu suka saki Ajiyar Numfashi,Hannayensa yasa yazagayo bayanta dashi,itako ta lafe bisa kirjinsa lokaci daya ta fashe da kuka,domin taji kasa control din kanta ne,.. Kanta yake shafawa zuwa bayanta da sigan lallashi yake Fadin"ShiiiI..Ki bar kukan nan don Allah,insha Allahu babu komai.."Yafada yana kara matseta ajkinsa,kukan natane ya lafa,ammh kuma ta sanya hannunta ta zagayo bayanshi dasu takara shigewa jikinsa tana kamkameshi sosai,Wani yam!Yum!yarr!Kawai yakeji gefe daya kuma tsausayinta ne da wani shaukin sha'awarta ke kara tumurmusanshi,Kasa rike kanshi yayu shima,baisan sadda yayimata tsautsaran riko ba yana Fitar da Numfashin wahala da muradi mai tsawo. Cikin fitan mgana ya Furta"Kinci abinci..? Kanta ta girgiza mai alaman a"a,yana tusa kanshi jikin wuyanta yake fadin"Meyasa..? yafada yana Fitar mata da hucin Numfashinsa awuyanta,wanda ya hassada mata wani Barin jiki mai hade da muradi mai girma,Kasa bashi amsa tayi saboda yadda yake ta shinshinanta gefe daya kuma duka hannayensa basu bar kara kaina ajikinta ba.. Fuskarta ya dago yana kallon kwanyan idonta,rintse ido tayi tana zubar hawaye wanda batasan dalilinsu ba,Harshensa ya Fito dashi baisan dalili ba kawai ya samu kanshi da kama kanta da hannayenshi guda biyu ya shiga lasheta mata hawayenta sai da ya lashesu tas,bayan ya tsotse harda saman idanuwanta inda gashin idonta yacika da ruwan hawaye,Karkarwa take tana kara shigewa jikinshi tana karban sabon sakon nashi,yaraf takoma ta lafe bisa kirjinsa kafin yakara dago Fuskarta yana kallonta Hannunshi ta rike tana kallonshi idanuwanta cikin so da zallar kaunarshi Yana kallonta idonta yakai bakinshi saman lebenta ya tsotsa,kafin ya sake maidashi kasa ya tsotsa,ya dago yana binta da wani sihirtattacen kallo,wanda yakara rikitata sosai,Lumshe idanuwanta tayi sanda ya kara dora harshensa bisa bakinta,da hanzari ta bude me ya saka harshensa ciki yana mata wani salon wasa wanda yake saurin Rikita ya"ya mata.. Harshenta ya cafke yana saraffashi cike da kwarewa da iyawa,Tuni Malika taji ta rikice,ta makalmaleshi tsab tana hakin maida Numfashi,shima kankame yake da ita yana shafa bayanta zuwa kugunta,yadda ta makaleshi ne,jikinta yayi laushi,tayi mai luu tana neman tagadasu su fadi,sai da ya riketa dakyau yana Fadin"Ki yi ahankali zaki kadamu fa.."Yafada cikin wani yanayi na bukatuwa. Batamai mgana ba,kuma bata sakeshi ba,ganin tna kara shigewa jikinsa ne,yasa ya saka duka hannuwanshi duka biyun ya dauketa cak,yafara tafiya yana kallon kwayan idonta,wanda ke cike da shauki,itama idonta na kanshi tana fata su dauwama ahaka,da tafi kowacce mace sa"a agidan Duniya. Bai direta ko"ina ba sai akan makeken gadonta ya kwantar da ita yana binta da kallo cikin wani yanayi,Kuru tayimai tana kallonshi itama kwayan idanuwanta suna chanza kala,kokarin tashi yake ta saka hannu ta rikoshi Ya dawo da karfi ya fada bisa kanta,ajiyar zuciya ta sauke kafin ta sanya hannunta duka biyu ta rumgumoshi ta kamkame tana Fadin"Plz don't let me go,Ina bukatarka akusa dani plz.."Take Fada tana goga fuskarta bisa kirjinsa,Mirmishi yayi kafin ya dago yana kallonta,hannushi ya saka yana Share mata kwallah yake Fadin"Nace miki bani Son yawan kukan nan ko? Indai ina raye i promise u Malika bazan sake bari kiyi kuka ba,ko wani ya bata miki rai ,nayi alqawarin dauwamar da Farinciki arayuwarki har abada,wanda ke neman bata miki kuma sai inda karfina ya kare.."Yafada idonshi na cikin nata. Wasu Hawayen Farinciki ne suka zubomata,wanda batasan sanda takara saka hannuwanta ta kamkameshi ba tana Fadin"I..I...I...."Take Fada ammh takasa fada saboda kukan daya tasomata,bai bari ta saki kukan ba ya dago da kanshi yanq Lasan haawayen Fuskarta kafin ya gangaro zuwa bakinta ya zura harshensa yana bata wani kiss mai zafi,nan da nan ta rikece ta rikeshi kam tana Shafa bayanshi da hannuwanta duk ta rikice... Bata kara rikicewa ba,sai da ya gangaro da hannunshi saman kirjinta,sai da tayi saukan Numfashi tana kara turomai kirjinta,Doguwar riga jikinta ya zame,duka Boobs din nata da suka cika suka bayyana dayake bata sanya bra ba,Rudewa yayi ya shiga murzasu da tafukan hannayenshi,itako tana kara Rike kanshi tana faman ya mutsa gashin kansa tana wani nishi kamar mai naguda. Bai barta ba,sai da ya sanya bakinshi yana mata wasa da harshensa akan nipple dinta cike da kwarewa,ai sai Malika ta hau bankaremai tana kara tusa kanta bisa kirjinta,ganin haka yasa yafara mata abun cikin zafi zafi,saboda shima yariga daya hau network din,cikin wannan halin ya raba Malika da doguwar rigar dake jikinta,shima ya cire nashi kaya,yakara hawa kanta dakyau,ammh yana yi da lura ssboda cikin jikinta,Tunda taji yana neman Ratsata,sai kuma jikinta yafara rawa,ta tuna da Abunda ya faru watanni baya,irin wuyar dataci,nan da nan jikinta yafara rawa,tafara Matse kafa,tana yarfe hannu tana wani marayan kuka. Ganin haka yasa yakai bakinshi gefen kunnenta yana fadin"Am srry..,Plz karki hanani samun natsuwa atare dake kinji..",Muryanta na rawa tace"Toh..Toh..Ammh ina..ina jin tsoro ne.."Tafada ko"ina na jikinta na rawa,Yana fitar da hucin numfashi yace"Zanyi miki ahankali wlh,am promse to be a gentle man kinji,juz close ur eyes kiyi huggging dina sosai.."Hannunta na rawa ta gyadamai kai kafin ta sanya hannunta ta kamkameshi,shikuma ya kifa kanshi bisa kirjinta bakinshi daya bisa boobs dinta yana tsotsa dayan kuma yana faman murza mata shi ba,Dahaka yasamu ya dinga Tura kai,ganin wajen ya kulle kanshi yasa ya Damke bakinta,danashi kafin ya tura kai da karfi gaske. Tunda ya sake jinsa aduniyar daya dade bai shiga ba,ai sai ya cigaba da aiki,tuni ya Fita daga hayyacinsa,Tun malika na hawayen azaba har takoma tana Tureshi da yakushi,ammh duk abanza baya jinta,Caccakarta yake kamar Allah ya aikoshi,Yana yi yana sakin wani Numfashi,bai saurara mata ba,sai da ya samu natsuwa har sau biyu kana ya Lafe jikinta yana sakin Numfashin dadi da wahala lokaci daya. Sai da yayi tsawon minti biyar kafin ya dago yana kallon Malika wacce tasha kuka,Mirmishin jin dadi yayi kafin ya sanya hannu ya rumgumeta yana Fadin",Tanque so much Allah ya biya ki kinji.."Yafada yana kai hannunshi saman cikinta yana Shafawa,tana jinsa ammh sakamakon bata da Karfin jikinsa yasa tayimai Shuru ganin haka yasa ya mike ya dauketa cak sai tiolet ya sakata Cikin bath,shi da kanshi yayi mata wanka kafin ya barta tayi wankan tsarki shima ya shiga yayi wankan tsarki kafin ya nadota cikin towel ya Fito da ita,barci ne aidonta yasa yana kwantar da ita ta bingere bisa gado tana barci,koda yazo har tayi nisa,Fuskarta ya shafa yana sakin mata kiss,akumatu kafin ya sake lullubamata blanket,aranshi yana jinjina zakin Ni"imar Malika mai maida mutum kamar bashi ba Bai kwanta ba,Sai da yakoma ya dauro alwala yazo ya shiga sallar Nafila,daga karshe yayi addu"an Allah yabama Malika juriyan karban wannan kaddaran data sameta akaro na biyu,yabata hakuri da juriya,Daga karshe ya roki Allah yabashi ikon rike Amanar da Mahaifinta ya barmishi na Dukiyarta da ita kanta,bai kwanta ba sai wajen uku,yazo ya Shige bargon bayan yasa hannu ya rumgumeta zuwa jikinta yanajin kaf duniya babu wanda yakaishi jin dadi awannan daren. -------------------------- karfe 5 na asuba wayar Sadiq tatasheshi daga Ni'imantattacen barcin daya kwasheshi,bayan sun gaisa Sadiq ya mai gaisuwa,daga karshe suka rabu kan in ya samu lokaci yau zai taho. Suna gama waya bai koma ba ya zare malika dake jikinsa ya sauko daga gadon,Wardrope dinta ya bude bayan ya jawo karamar akwatunta ya Shiga diban kayanta yana sakamata,Bai kwasa da yawa ba,sanin da yayi achan gidan ma bata rasa wasu kayan,ammh duk da haka ya sanyamata duka abubuwan da zata bukata,Fita yayi daga dakin nata,zuwa nashi shima cikin wata karamar jaka ya saka kayanshi kala uku,Tunda yana Tunanin da anyi uku zai dawo saboda aiki Kafin ya dawo dakin ya amsa wayoyi da dama,masu kiransa su masa gaisuwa ciki harda Zahra Da Nadiya wacce sukace A BBC sukaji,daga karshe zahra tace yabama Malika ta mata gaisuwa,baki ya rike aranshi yana jinjina Shigen rawan kan Zahra,sanar da ita yayi tabari ba yanzu ba sai zuwa gobe zai bata ta mata gaisuwa bata damu tace toh shikenan,dahaka sukayi sallama. Yana Shigowa ya tarar da Malika tatashi tana waige waige shi take nema sai gashi ya Shigo..Kuri tayi mai da ido tana kallonshi,shiko Hannayensa ya saka cikin aljihun dogon wandonsa na barci yana kallonta Lumshe ido tayi tana Tuna Abunda yafaru jiya,kafin ta bude tana jin kamar amafarki ne,bata samu zarafin mgana ba,taci karo da karamin akwatunta daya Shiryamata kayanta aciki Bin akwatin tayi da kallo gabanta na Fadi muryarta na rawa tace"Wannan akwatun fa mallam.."?Kanshi tsaye yace mata "Katsina Zamu..."Jin Abunda ya fada yasa zuciyarta ta tsinke da azama ta yaye bargon jikinta ta diro daga saman gadon,har towel din dake jikinta na neman Faduwa tace cikin rawan murya da Sigan Tambaya"Katsina kuma...? Tafada tana sanya idonta anashi. Kanshi ya daga mata cike da jarumta don yana son yanzu ya sanar da ita Abunda ke Faruwa kafin su isa,Hannunta bisa saitin zuciyarta tana Fadin"Wani abu yafaru ko? ko wani abu zai Faru,Tun jiya naji ajikina wani abu na Faruwa.."Tafada hawaye na wanke mata Fuska,Saurin karisawa yayi gareta yana fadin"Waya ce miki wani Abu ya faru. ? Dagowa idanuwanta tayi da suka kada sukayi jawur tace"Karka sake cemin babu Abunda ya faru,Mallam in babu Abunda yafaru me zamu je muyi a katsina harda kaya kuma,Don Allah ka sanar dani Abunda ya faru da Daddyna ni musulma ce kai ka koyar dani yarda da kadaddara mai kyau ko mara kyau..",Takarishe cikin gunjin kuka Tuni tsausayinta ya lullubeshi da hanzari ya jawota jikinsa ya Rumgume yana lallashinta cikin tatattausan kalamai,,Tunda taji yafara Mata Nasihan yin hakuri da rayuwa tare da sanar da ita mutuwa dole ce ga duk bawa Tunda harta monzon Tsira salallahu alahi wasallam ya dandani Dacin mutuwa to kowama aduniya sai ya dandaneta,Jikinta ne yakama rawa ta dago daga kirjinsa tana fadin"Dad...dadd..Ya..aa rasu ko.."?Tafada bakinta da jikinta na rawa kura mata ido yayi shima yana jin kwallah ta cikamai ido,bai iya kallonta ba,ya Gyada mata kai yana Fadin"Allah ya karbi Abinshi malika domin yafimun sonshi,jiya ina asibitin Allah yamai cikawa,ya rasu yana ambaton sunanki tare da rikon na rike mishi ke Amana bisa gaskiya ya rasu yana Farincikin yabarki hannun na gari..." Har yagama mgana bata kara motsi ba,illah wasu tawayen hawaye dasuke mata barin makauniya bisa fuskarta,kyam take kallonsa bakinta na wani karkarwa,lura da hakan da yayi yas,kamata da karfi tana kokarin Fizge kanta ya tusata cikin kirjinsa yana Fadin"A"a kar miyi haka dake ,Yanzu kika gama sanar dani kin yarda da kaddara mai kyau ko akasinta,ki daure zuciyarki kiyi kuka na salama,Indan kin rasa natsuwarki kiyi ta maimaita innalillahi acikin zuciyarki insha Allahu zaki samu ramgwane..."Kukan daga karkashin zuciyarta ya Fito da karfinshi bude baki tayi ta sakeshi tana wani kamkame shi kamar zata kadasu,.. Kyakyawan riko yayimata yana Faman bata baki,ammh ina haka take wani kukan gwanin ban tsausayi,Neman take ya saketa ta zube kasa,yaki sakinta sai ma kokarin Dago Fuskarta yake taki yarda Muryanta har ta Dishe saboda kuka fadi take"Daddylove din nawa ne ya rasu..? Wayyo Allah na!Na shiga uku yanzu bani da kowa..Wayyo ni Malika..!Take fada kamar zata Shide,ganin haka yasa ya toshe mata baki da bakinshi yana kissing dinta cikin gaggaawa,itako Fuskarta yana ta barin hawaye,sai da yakara lashe hawayen nata tas kana ya saki Fuskarta yana maida Numfashi,kamar yar maye haka takoma bisa kirjinsa ta lafe bayan ta kamkame shi tana wani shessheka. Bayanta yake Shafawa yana Fadin"Take easy Malika,Kidaina fadin baki da kowa karki yi sabo,kina da Allah kuma kina da ni,ga su Abbi wanda na tabbata son da suke miki bai kai wanda sukemin ba ni da suka haifeni.,NAYI MIKI ALQAWARIN BAZAN BARI KIYI KUKA BA,MATUKAR INA RAYE TARE DAKE.."Yafada yana kamkameta saboda yadda take Fitar da sautin kuka,Yayi ta lallashinta yana mata nasiha,yana cemata ba kuka yakamata tayima Daddy ba,yanzu yafi bukatar addu"arta fiye da komai. Dakyar ta yarda ta bar jikinshi ya zaunar da ita gefen gado zai shiga tiolet ta riko hannunshi,cikin sanyi jiki ya waigo yana kallonta,Idanuwanta da suka kala ta sakamar kafin tace"Yaushe Daddyna ya barni mallam..? Hannunta ya kama ya damke cikin nashi cikin taushin murya yace"Jiya da daddare,Daren da kika ga nayi ai chan naje,da rana Abbi yakirani yake sanar,tashin hankali ne yasa ban dawo gida ba,na wuce daga chan,..."Runtse ido tayi hawaye suna zubomata kafin ta bude tana Fadin"Yaushe za"a yi jana'izarsa..?Yana shafa bayan hannunta yace"Yau da misalin karfe 11 saboda bakin nesa da zasu so..,Shiyasa nake so mu tafi da Wuri.."Bata kara mgana,sai ma kokarin mikewa datake,ganin tana rawan kafa kamar zata kife yasa yayi hanzarin rikota ta fado jikinsa yadagata cak,ya shiga bayin da ita,Kasa komai tayi sai dai Shine yayi mata wanka anayi tana kuka,kyaleta yayi don yasan har abada bazai hana ta kuka ba. Bai barta ba sai da ya wanketa tas,yanadota a towel ya maidota daki ya saukar da ita kan gado yana binta da kallo,duk hawayen da zai zubo mata shi zai sanya hannu ya sharemata yana lallashinta,shi ya shafamata mai yana yaba kyau da tsari na jikin malika daga cikinta har wajen babu abun yarwa,yadda yakeji kamar yakara kafin su tafi,buh halin datake ciki kadai ya dakatar dashi,Kallon dan cikinta kawai yake wanda keta motsi yana gani,shafa cikin yake yana kallonta cike da tsausaya,itako idanuwanta na Rufe tana rike hannunshi tana sakin nishi lokaci daya da hawaye. Da kanshi ya Shiryata cikin doguwar riga cikin kayan daya dinkamata ne,ya sanya mata dankwali da hijabi,Agurguje yakoma dakinsa yayi wanka ya Shiryo cikin wata shadda ash colour,yana sanya hulansa zanna bukar ya Shigo dakin yace tatashi suyi sallah,ganin kamar jiri take gani yasa yace tabishi sallar daga zaune,haka akayi Azaune tayi sallar tana sharan kwallah gwanin ban tsausayi,suna idarwa da kanshi ya kimkimin akwatunta da yar jakan kayansa zuwa mota bayan ya dawo ne yazo ya kamata ganin tana tafiya dakyar ne yasa ya kuramata ido yana fadin"Are u okey...? Kan kirjinsa ta lafe tana gyadamai kai,cak ya dauketa har cikin mota ya ijiyeta kafin yakoma cikin gidan ya kakakkashe duka na"uran wutan gidan bayan ya kulle kofar babban Falon gidan kafin ya Fito,wajen megadinsa ya nufa bayan sun gaisa yabashi key din yana sanar dashi rasuwar baban Malika,maigadi nata kwararo addu"a yana sanar da Saleem yanzu yaji sanarwan aradion. Komawa motar yayi ya shiga yana Daura set belt,itako ta sanya kanta tsakanin cinyoyointa tana kuka bai mata mgana ba,ya shiga karanta addu'ar da Annabi muhammed (SAW) ya koyar damu in zamuyi tafiya bisa wani abin hawa,kai tsaye yatada motar yana zubama megadi hon wanda ya wangalemai get da hanzari ya sulala waje yana musu fatan Allah ya kiyaye hanya yakuma bada hakurin rashi Ameen. *Momyn ladingo ce* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Dis page is For u *MY BEST*😘Endless of love Besty_ *21* Karfe 10 da wani abu suka isa anguwan su Malika,wanda Tundaga farkon layin har karshe jerin gwanon motoci ne na gani na Fada,anguwan tacika makil,Malika ko Tunda suka baro Zamfara take kuka har zuka iso katsina,Tun Saleem na bata baki har ya gaji ya kyaLeta. Bai samu damar Shiga da motar ciikin haraban gidan ba,sakamakon yadda aka wangale get din Mutane sunyi Dafifi kowa nata daura alwala saboda lokacin Jana'iza ya kusa,Malika dataji kanta na sarawa ta dago kanta tana bin ko"ina da kallo,Zuruf tayi zata bude Murfin motan sai taji hannun Saleem bisa nata ya damke,waigowa tayi tana kallonshi wasu hawaye suna zubomata Kara damke hannunta yayi yana kallonta kai tsaye kafin yace. "Kiyi min wata alfarma plz..? Girgiza kai tayi tana Kokarin kwace hannunta,shiko yaki sakinta ganin haka yasa ya Bude baki yana Fadin"kada ki yi kuka sosai,kinga fa Tundaga Zamfara kike kuka,har muka iso nan,don Allah in kika Shiga ciki ki tararro juriyanki kada kiyima Daddy kuka,ayanzu haka yafi bukatar addu'anki Fiye da na kowama.."Runtse ido tayi hawaye suna kwaranyomata kai ta gyada mai alamun taji,mirmishin yake ya saki kafin ya Kai hannun nata bakinshi ya sakarma wani light kiss,kafin ya saketa ta bude murfin motan da hanzari Ta fice tana Rufe Fuskarta da Gefen hijabinta kuka na kwace mata. Shi kuma ya Fito daga motan ya nufi haraban gidan inda su Abbi ke tsaye shida sauran yan"uwan Daddy na Malumfashi,gaisawa sukayi yana kara musu gaisuwa,kafin shima ya koma gefe yasamu buta yafara daura alwala domin har an kammallah yima Daddy Sutura ana jiran lokaci ne ya cika a sallaceshi zuwa gidansa na gaskiya,kowa ka kallah awajen Fuska babu Annuri kowa yayi tagumi yana alhinin wannan Rasuwa ta Alhaji Abdulmalik Dankasuwa.... Itako Malika na Shiga Falon gidan ta tsaya cak tana bin kowa da kallo,gabadaya dangin Daddyn natane yan malumfashi suka cika Falon suna koke kokensu,wanda ada sune in ta gansu sun zo gidansu tayi ta fadan cewa sun zo maula sun cika musu gida,sai gashi yau sune suka zo su taru suyi kukan rashin da kuma Faduwar bango garesu gabadaya. Nan idanuwanta suka kai kan Hajiya binta dake zaune gefe da dogon Hijabi ta carbi tana ja,Fuskarta ta kumbura saboda kuka,gefenta kuma Joda ce itama sanye da hijabi tana Sharan kwallah,Shigowar Malika shiya sa Falon ya dau Shuru kowa ya juyo yana kallonta cike da tsausaya domin ansa babu wanda akama mutuwa kamar ita. Hajiya ta kalleta idanuwanta da suka sukayi jawur cike da kuka tace"Malika.."Takira sunanta cikin raunin da karayan zuciya,ai da gudu malika tatafi gareta ta Fada jikinta tana Fashewa da kuka,Rumgumeta hajiya tayi itama kukan take tana Fadin"Mun rasa Alhaji malika,mun rasashi lokacin da da ni dake muka fi kowa bukatarshi,wayyo Allah mutuwa tamana yankan kauna ta daukemana Alhaji lokacin da muke tsakar bukatarshi.."Take Fada tana kuka,Malika dake jikinta ta kara fashewa da kuka,cikin muryan kuka wacce ta Dishe take Fadin. "Dama da gaske mallam yake Daddylove ya tafi ya barni..? Why..? meyasa zai min haka ? zai tafi ya barni cikin wannan Duniya mai cike da kunci ni kadai,ya rayuwata zata kare,wayyo ni Malika dama Allah ya dauki raina,nima na mutu abinne gawata kusa data Daddyna,domin babu Abunda zan tsinta aduniyar indan na zauna ba ni da kowa sai shi,gashi yanzu Babu shiii.."Tafada tana kara kife kanta akasa tana kuka harda jijjiga. Wata wacce take kanwa ga Daddy tataso daga inda take ta riko Malika itama tana hawayen tace"Ashh malika bar Fadin irin wannan kalaman basu dace ba sam,ki na zaton Allah daya bamu shi bai Fimu sonshi bane? karki Manta gawan Mahaifinki na cikin gidanan kuma sai ki sakamai da mganganun banza da koke koke,yanzu ne fa zamu nuna mai mu masoyanshi ne ta hanyar neman masa gafaran Allah,gashi kema baki da lafiya ko so kike kijama kanki mtsala muna alhinin rashin Mahaifinki mukoma alhinin shiganki wani hali..? Girgizamata kai Malika tayi tana toshe bakinta da hannun kada kukanta ya Fito,Zaunar da ita tayi tana zama kusa da ita carbin hannunta ta mika tana Fadin",Yita salati acikin ranki,Kibar kukan nan hakannan kada kijama kanki wata mtsalan Abdulmalik tashi ta kare ,sai dai mune muke cikin kila wa kalan Yaushe zamu mutu? yau ne gobe ne? bamu sani ba.."Take Fada tana Share kwallah. Gabadayan Falon sai da kalamanta yasasu ta kwallah,itako Malika batayi gaddama ta karbin chasbawan tana karanta innalillahi bakinta na motsi ammh hawaye sun gaza daina gudu bisa kuncinta,haka Hajiya binta ma ana ta bata baki,ana mata Fadan tadaina kuka ita da zata Tallafin Raunin malika,ammh itama ta koma tana biye mata suna kukan da bashi da amfani,dole suka hadiye kukansu ammh fa zukata sun Raunana,gabba sun yi rauni suma. Tashin hankali bai kara ziyartansu ba sai da akace Hajiya da Malika su fito su zo Falon waje inda aka shirya Daddy,domin sumai addu"a da ganin karshe,lokacin da Malika taci karo da gawan Daddynta kasa control din kanta tayi haka ta fada kanshi ta kamkameshi tana kuka mai taba zuciya kamar zata Shide,hajiya ce kadai ta samu daurewar yimai addu"an Fatan dacewa da kyakyawan mtsayi. Malika kin sakin Gawan Daddy tayi Fadi take ita, Daddynta bai mutu kada su Fitar dashi,gashi ta rike makaran dakyau taki saki,sai da Abbi ya fita waje ya kira saleem yazo da karfi gaske ya bambareta jikin makaran yana lallashinta,ammh ita hankalinta ya bar jikinta,ganin tana Fizge fizge ne yasa ya Kara tsaurara rikon dayayi mata,har sukayi baya suna neman Faduwa,neman kwatan kanta take ita sai taje ta riko daddynta kada su Fita dashi,ammh Saleem bai barta ba sai da ya tabbatar da sun Fita da gawan waje kana ya Sausauta rikon nata yana Fadin"Haka mukayi dake..? Haba Malika stop don Allah baki ganin halin da kike ciki ne?"...Yafada yana kallonta cike da tsausayinta. Kuri tayimai kafin kawai yaga tayi luu zata Fadi ya tarota yana Salati,ashe suma tayi sai da wadanda ke kusa suka taimako da Ruwa ya Shafamata kana ta Farfado,wannan karon babu kuka da baki sai dai kukan zucci da Fitowar hawaye,kamar an bude fanfo ammh ba mgana,Gashi ta makaleshi gam taki sakinshi,dakyar ta yarda ta koma jikin Joda,ammh sai da ya ce mata zashi jana'iza ne da an kai Daddy gidanshi na gaskiya zai dawo gareta,kana ta sakeshi ya Fice kamar ya mata kwallah. Amsallacin jumma'an dake anguwan aka Sallaci Daddy,wanda ya tara dimbin jama"a iya kallanka mallam,agaskiya Daddy ya dace kama daga yadda Annabi ya kwatanta mana Dacen musulmi na kwarai,uwa uba ga Shedan mutane daya samu Abun sai wanda yagani,Amgakabarta ko ba"a matsaka tsinke wasu ma har aka binneshi basu hango ba,saboda tsabar jama"a,Saleem yana daya daga cikin shakikan Daddy wadanda suka sanya kanshi cikin kabari suka turbene da kasa,saboda imanin da Tunanin shima watarana nan za"a kawoshi yan"uwanshi na jini na gani zasu Rufe kanshi da kasa,kai Allah ka Shirya damu kasa mu dace Duniya da lahira. Bayan an kaishi gidansa na gaskiya aka dawo ana cigaba da karban gaisuwa bayan an saka Rufunan manya manya cikin haraban gidan da waje saboda mutane,Su Abbi sune gaba gaba wajen karban gaisuwa,Saleem ko yana tare da Sadiq dayazo bayan angama jana"izar Daddy,da wasu yan'uwansu matasa irinsu yan malumfashi,Ba dadewa sai ga su Ummi sun iso,har cikin gida suka shiga inda suka iske malika zaune inda Saleem ya barta tana kwallah ammh ba"a mgana,Ummi ta zauna kusa da ita ta Rumgumota tana ta lallashinta da mata nasiha masu ratsa jiki,hakama Hajiya itama ta dora danata hadda hajiya binta basu kyale ba,suna ta bata baki,don babu shakka mutuwar Alhaji itama ta daketa. Sai yammah kana su Ummi suka koma Abuja,haka akacigaba da amsan gaisuwa daga bangarori dadama,ciki harda manajojin gidajen man Alhaji Abdulmalik dankasuwa,tare dana kamfafonimshi,Malika kuwa tunda aka Fita da gawan Daddy bata kara ma kowa mgana ba,sai dai kawai aga hawaye suna zubomata,sallah kadai ke tada ita daga inda take,Abinci ma In Joda ta matsa mata taci sai kawai tarashi ta Shige tiolet ta kulle kanta tana kuka,data gaji da halin data ke ciki ne ta Fita waje taje ta sanar da Saleem,shima Hankalinshi tashe yazo yana magiyan Ta bude,ammh malika taki,yayi yayi,sai ya koma daga ban baki zuwa yimata Fada cikin zafi,ammh kememe Malika taki budewa kuma yanajin kara sesshekan kukanta,wanda ke tafasa mai rai. Kada kai kawai yayi ya Fita daga dakin bayan ya Umarci Joda data rabu da ita ta samu natsuwa zata bude da kanta,haka ko akayi sai da tagaji da zaman bayin kana ta Fito tana goge kwallah,ganin ban tsausayi ga cikinta ya girma Tunda ya Shiga watanshi na bakwai kenan,sai daddare kana Malika ta iya shan madaran hollandian da kaza,shima Saleem ne ya ritsata kuma ya matseta ya dinga Turamata abaki,bayan ya gama yakoma aikin lallashi,tana Rumgume ajikinsa,Joda dake kula da Malika in ta gansu awannan yanayin sai ta dinga mamakin yadda aurensu ya kasance,ammh kalli yadda Saleem yake kafa kafa da malika Bayason ya barta tana kuka,Baya barinta sai ya tabbatar da ko bata bar kuka ba toh hankalinta ya kwanta,ta bar koken koken takoma tana ajiyar Zuciya. Ranar da"akayi sadakar ukune sai ga Maman Abba ita da megidanta sun zoma Malika da Saleem gaisuwa,Zahrin gaskiya Malika taji dadi sosai haka ta Rumgume Maman Abba tana Fadin"Maman Abba kinga yadda Rayuwata tadawo ko? Babu uwa,uban dani ke kallo amtsayin madubina shima yatafi ya barni.."Take Fada tana kuka,bayanta Maman Abba ta shiga bugawa tana Fadin"Kina da wani Madubin Malika,mijinki shima bangon kine,ina mai tabbatar miki Allah bazai dauke Daddy kuma yahanaki soyayyar Saleem da kulawanshi ba,sai dai ya daukeshi don gwada imaninki,kiyi tawakalli sai kiga Allah ya Dubeki da idon Rahama ya haska rayuwarki,wanda Daddy na cikin kabari Allah zai nuna mishi ke,kuma yayi alfahari dake.."Kalaman Maman Abba ya sanyayama malika rai har sai da ta murmusa tana digan hawaye,sake Rumgume juna sukayi tana kara lallashinsa. Joda dake gefe kuwa sai tayi mamaki ganin yadda Malika ta saki jikinta da Maman Abba,wacce ke ta bata baki tare da wasu shawarwari,Itako Malika sai gyada kai take tana nuna alamun gamsuwa,sai yammah sukayi Shirin tafiya,Har waje Malika ta rako Maman Abba tana mata godiya,wanda ganinta haka bakaramin Dadi Saleem yaji ba,kura mata ido yayi yana kallonta,Itako kallo daya tayimai ta kauda kai tana Jin kunya ganin Abokinshi Sadiq na wajen ga sauran Manyan mutane irinsu Abbi. Suna sallama da Maman Abba,shiko Saleem shida Sadiq suna musabaha da Baban Abban,ammh kacokan hakalin Saleem naga Malika ganin yadda kawai yaga ta wani rame,kodon bai kara ganinta cikin rana bane,? Sadiq ne ya lura da kallon da yake mata,shima ya kalleta aranshi yana yaba kyanta ba karya,har motar su Maman Abbah ta Fice daga gidan bata koma ciki ba ita da Joda,Ganin haka yasa Sadiq ya zunguri Saleem yana Fadin"Haba Acp wannan dogon kallon ai ya wuce na Shari"a.."? Wani banzan kallo ya jefamai kafin ya cigaba da kallon Malika so yake su hada ido ita kuma tana lura dashi sai taki yarda,dariya Sadiq ya Sheke dashi kafin yace"Kuma gaskiya Ba laifi Matar naka akwai kyau,gata jinin Turawa ko banza zakuyita haihuwan Jajayen Fata kyakyawa.."Saleem bai san Dalili ba,kawai yaji mganar Sadiq ta cakanmai rai sosa,wani takaichi ya kumeshi,Kirne Fuska yayi kafin ya fara takawa zuwa kusa da malika wacce ke Shirin juyawa zata koma gida,bai ce mata kala ba,ammh yana biye dasu har suka Shiga Falon gidan,wanda joda ta dingama Malika radan ga Saleem nan na binsu abaya,bata juyo ba,ammh ita kadai tana Sakin mirmishi domin da babu Saleem arayuwarta wannan Rashin ya faru,kila itama da yanzu tana kwance,shiyasa akowani lokaci take jinjina ga gwarzon maza Wato Saleem domin ya zama zakara ne acikin zaratan maza. Sai da yaga sun Shige kana ya dawo wajen Sadiq yana kallonshi duka hannunwanshi cikin aljihunsa yake Fadin",Dazu kace ina kallonta? matarka na kallah ko matata? kuma dakake yaba kyanta uban wa yakai idonka Akan matata? plz mallam wlh karka kara,In so kake ka yaba kyan mace sai kayi aure kaga sai ka yaba naka..."Daga haka yayi Wucewarsa zuwa Rumfar dayake zaune,shiko Sadiq baki ya rike yana Fadin"Au abun harda gori,toh muna kwana nawane inda rai da rabo. Washegari sai ga Baban Zahra yazo gaisuwa wato tsohon Alkalin alkalai na kasa gabadaya,Zahirin gaskiya Saleem yaji dadi sosai wanda har cikin gida ya shiga dashi yayi ma hajiya da Malika gaisuwa,bai jima ba ya Tafi,bayan tafiyan ne Sadiq da Abbu suma suka dau hanyar Abuja bayan ya Shiga har ciki an kiramai Hajiya Binta da malika yayi ta musu Nasihan mai ratsa jiki,wanda ta Shigesu,haka suke hawaye kawai don yadda zukata suka raunana babu wani abunda baki ya isa ya Furta,gashi tun yau hudu da rasuwar Daddy mutane duk sun fara watsewa za"a barsu su kadai Abun yazo ya rafkesu. Sun tafi ba Dadewa Saleem ya nemi gnin Malika,ganin da Jama"a sosai a baban Falon gidan nasu gashi ita kuma tana sama ne,ita da joda,sai Yan alqawarin nata mery da Dose,Umartan Joda tayi data bude mata wani falo dake ta waje ya shigo,aiko haka akayi Joda ta bude Kofar Falon Saleem ya Shigo sai ga Malika ta Shigo da cikinta gaba,tana sanye da wata doguwar riga mai Tsukakken hannun kamar roba. Batama kariso ba ya isa gareta ya riko hannunta suka zauna bisa daya daga cikin kujerin Falon,kura mata ido yayi ita kuma kanta na kasa,ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Ya hakurinmu..? fata dai kinci abinci baki zauna da yunwa ba..? Kai ta gyada mai kafin tace"Hakuri mungode Allah..'Tafada idonta na cikowa da kwallah,Baki ya sake kafin ya dafa duka kafadunta da hanuwanshi biyu yana Fadin"Toh kuma miye Abun kuka? ashe bakijin mgana na,har saunawa zan fadamiki kuka bashine zai dawo da Daddy ba,yatafi kenan sai dai mu tayashi da addu"a Allah yasa chan yafiye masa nan.."Hawayen datake rikewa suka zubomata ta sanya hannu ta share tana Fadin"Na bari insha Allahu..'Tafada cikin wani yanayi. Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Dama na nemi ganinki ne,saboda ina so na Wuce zamfara yanzu,shine nake so na tambayeki ranar bakwai zaki koma gida,ko kuwa sai kin kara wani satin..? Dagowa tayi tana kallonshi cikin Rauni tace"Yau kuma..? gyada mata kai yayi kafin yace"Eh Tun jiyama naso tafiya,so rashin Tafiyar su Abbi ajin ne shi yadakatar dani,."Jikinta ne yayi sanyi kwal kwal da ido tana so tayi kwallah,bata fuska yayi kafin ya nunata da yatsa"Karki kuskura hawayen nan su zoba..,Haba don Allah ya kikeso nayi da raina ne,Kullm kuka kullum kuka,Ehe ko kin taba tambayanta yadda kukanki ke kona kin rai ehe..? Yafada yana sakarmata manyan idanuwanshi. Rudewa tayi ganin yadda bacin ranshi ya Fito sarari,Kukan take son hana kanta sai kawai ta fada jikinsa da karfi tana tura kanta cikin Faffadan kirjinsa,tana hana kanta kukan dayakeson kwacemata, Riketa yayi saboda tabashi haushi,ammh jin yadda take kara kamkameshi ne yasa ya tabbatar da hakuri take bashi,hannuwansa yasa duka biyun ya Rumgumota yana Sakin ajiyar zuciya yake Fadin"Toh wai miye na kuka daga nace zan Tafi yanzu? kodai baki san na tafi ne..? Dagowa tayi ta daga ga mai tana kokarin maida hawayenta,Zuru yayi mata da ido kafin yace"Meyasa baki san na tafi,alhalin kinsan cewa zan koma bakin aiki.."Rau rau takara yi kafin tace"Kabari sai gobe ka tafi don Allah..!Ina son kasancewa tare dakai.."Tafada tana maida kanta jikin kirjinsa Rumgumeta yayi yana sakin wani munafikin mirmishi,Shafa bayanta yake yakasa mgana Lokaci daya ya dago kanta yana kallon kwayan idonta,Kasa juran kallon tayi sai ta hau lumshe ido tana kokarin maida kanta kirjinsa,Bai bata dama ba,sai ma Lebenshi dayakai kan lebenta yana tsotsa cikin wani salo,bata mai gaddama ba,sai ma kara rikeshi datayi tamikamai Harshenta ya kama yana tsotsa cike da kwarewa, kan cinyarsa ya maidata,shikuma ya cigaba da kissing dinta yana Shafa ko'ina ajikinta musassaman cikinta zuwa kasan mararta,Tuni ta Birkicemai lokaci daya itama take maida mai martani tana shafa kanshi zuwa bayanshi hannayenta na kara kaina bisa kirjinsa tana shafa kan Nipples dinshi,Shan yaji Saleem yafarayi saboda jin wani abu na zirgamai,Lafe mata yayi ajiki yana maida Numfashi,hannayeta ya rike cikin wani yanayi yake Fadin"Bari kina tadamin da hankali.."Yafada yana kamkameta cikin wani yanayi. Da idonta wadanda ke cike da bukatuwa ta kalleshi,shima ita yake kallo batayi musu ba ta daina tabashi,ammh sai ta kai bakinta saitin Kunnanshi tana Fadin"Am here for u Only mallam.."Tafada tana Shafa keyarshi da hannunta guda daya jin haka yasa ya Birkitota yana kallonta da idanuwansa wadanda suka chanza launi yace"Really...."Yafada cikin wani Shauki kunya ce ta kamata sai ta kauda kai tana kokarin tashi daga jikinsa bai bata dama kawai sai ya mikar da ita tsaye,bai mata mgana ba ya koma ya kulle kofar falon yana dawowa ya Cire riganshi yana kallonta ido cikin ido,kafin ya sanya hannu ya zare mata hijabin jikinta yana binta da kallo,Wuyan doguwar rigar ya sabule mata dama tana babban Wuyane,sai gata tayi kasa zata fadi,da hanzari ta rikota tana kallonshi Shishige mata yafarayi yana wani kankance ido,Tokareta yayi da kafarsa hade da kujera yana kama Fuskarta da hannu biyu yashiga bata wani kiss mai zafi yafi minti biyar yana tsotsan bakinta kafin ya Kwantar da ita ahankali bisa kujeran shima yazo ya kwanta akanta,ammh sai yayi gefe saboda cikin jikinta,Tana kallon kwayan idonshi ta dauki hannunshi ta aza bisa boobs dinta,kafin ta rumgumeshi tana Shafa kirjinsa cike da salo da kwarewa,cikin lokaci suka rikita juna bakacin sautin komai sai na tashin Numfashinsu,Saleem yasamu Abunda yakeso,Rumgume yake da ita yana maida Numfashi Dadi da wahala lokaci daya.. Saboda jaraba irinta Saleem da samun waje kakumarta yasake yi,Yakara second round,domin kwata kwata baya gajiya da tsaga jikin malika tana da wani sirri dake rikitashi sosai wanda ko yanzu yagama Having Sex da ita,toh sha'awarta zata dawo mai sabuwa,sai gashi tare sukayi wanka a bedroom din dake dakin dama akwai bedroom Saleem ne yake ra"ayin yau din Asaman kujeran za"a kashe arnan😂🙈suna gamawa Ya je mota ya Dauko kayanshi ya sauya kafin yakoma ciki yayi ma su Hajiya sallam,kunga Malika yadda ta makaleshi gabansu Hajiya da Joda da yan Malumfashi tana kuka Wurjajan,Wai bazai tafi ba,shi yau yaga ikon Allah,Dakyar da Sodin goshi ya lallasheta ta sakeshi shima sai da yayi mata alqawarin Ranar bakwai zai zo ya ganta,duk da haka bata ga tafiyarshi ba daki ta koma tana kuka,shikanshi jikinsa ba Dadi ya tafi bai san dalili ba yanaji kamar Malika ta dauwama dashi har karshen rayuwarsa ba,bai yi Kukan rashi da kewarta ba sai da ya koma gida yayi kwance kan gado yana Tunaninta,Zahra ko tana ta nacin kira yaki daga kiranta saboda in yana cikin halin Kewa da Tunanin malika baya bama komai muhallin hanashi ko dakatar dashi. _______________________ *BAYAN KWANA BAKWAI..*. Ranar addu"an bakwai da Wuri Saleem yazo,shima Abbi yazo shida Ummi ammh basu jima ba suka tafi,shima saleem bayan gama addu"ar yace joda ta kiramai Malika shi zai koma,Kin fitowa tayi tana chan saman dakinta tana kuka,dole tasa Saleem ya Shiga har saman da kanshi yadda ya ganta Abun bai mai dadi ba duk takara ramewa akan yarda ya barta Ranshi ya baci ya fara mata Fadanshi da bataso,Ai sai ta Rude ta sauko daga kan gado tana bashi hakuri ammh yayi banza da ita ta inda yake Shiga batanan yake Fita ba,daga karshe yace indai tana mai Taurin kai Allah bazasu shirya ba. Hanyar Fita yakama da hanzari ta mike ta isa ta bayanshi ta Rumgumoshi tana kuka take Fadin"Don't leave me..Don't.."Take Fada tana kuka cak ya tsaya yana jin kukanta na ratsa ranshi,Juyo wa yayi yana Riketa da wani karfi ta fada jikinsa ta kamkameshi tana kuka,Shima maida hannuwanshi bayanta yayi yana sakin ajiyar Zuciya,Shafa bayanta yake zuwa kasa Tudun hip dinta cikin wani salon lallashi yake Fadin"Fisabillahi Yanzu Abunda kikeyi daidai ne? Sau nawa zan fadamiki Kidaina wannan koke koken,? Kokuwa dai wulakanci da kuma raini ne ke damunki Tunda nace bani son kukanki wato in mutuwa zanyi na mutu ko..?"Da sauri ta dago kanta tana girgixamai tana hawaye,hannu ya sanya ya Sharemata hawaye yana fadin"I already tell u no more kuka indai ina tare dake,to meyasa kike yi koda yaushe.?."Tana rike hannunshi tana kara share kwallah tace"Nabari..Nadaina wlh.."Tafada cikin sanyin murya,Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya Rumgumota jikinsa yana kamkameta Idanuwansa suna Rufe yaji ta Furta"I miss u..."Shikanshi Shaukin kewarta ne yasa ya Furta mata"Me tooo..."Cikin muryan So da muradi. Bai mata komai ba ranar ammh kafin yatafi sai da yalugwigwitata son ranshi,Kuma yayi mata wanka ya bata abinci kafin ya tafi ya barta wajen Hajiya da joda zuwa wani satin yazo ya tafi da ita,bai bari tasan tafiyarshi ba daga Fita salla ne bai dawo ba,sai dai ya kirata awaya yace yatafi,saboda yasan sai tayi kuka,shikuma kukan tane sam bayaso,Akwai sunsha kuka ranar ita da hajiya barima da duka jama'ar Malumfashi duk suka koma aranar ko mazan dake waje ba kowa,Tuni kowa ya watse,wadanda suka tsaya shakikan Alhajin ne Na Malumfashi,ranar mutuwar ta dawo musu sabuwa gida yayi rakwa rakwa,ranar Malika da zazzabi ta kwana saboda kuka,da Joda ta mtsamata tasha panadol taki sai tace mata zata kira Saleem ai da hanzari tatashi da karba tasha takoma ta kwanta tana maida numfashi lokaci daya da hawaye,itako Joda sai da murmusa tana yaba tsarin wannan Soyayyar mai cike basarwa domin duk wanda ya kalli malika yasan Tana cikin mayen son mijinta,haka shima soyayyar Malika bata boyiwa acikin idanuwansa ba,sai dai shine yake kokarin boyeta da karyata kanshi da wai amanace gareshi gata marainiya ba Uwa ba uba. Haka suka ciga da zama ita da hajiya da joda Da su merry wanda zuwa kwana goma kowa ya watse sai wata goggo talatu kanwa take ga Hajiya suma zaune tare,Tun zuciyoyi na kuka suna bayyana digan hawaye har suka gaji suka dau dangana suka koma kukan zucci,Ranar da Daddy ya cika kwana 14 da rasuwar tun Safe Malika tayi Shirin komawa ita da Joda wanda Hajiya tace su tafi tare ta rinka taimakamata da wani abu saboda yanayin Jikin na malika,aiko taji dadi sosai,Saleem ya kirata yace Direba yakawo ta shi bazai samu zuwa Meeting suke dashi.. Da zata tafi haka ta kamkame hajiya ta kuka dakyar aka bambareta daga jikin hajiya,wacce itama kukan mutuwar ta dawo mata sabuwa,mota kawai Malika ta Shige tana kuka mai ban tsausayi dayake dama already sun Saka duka akwatun nan kayansu cikin booth din motar wanda Direba zai kaisu,cikin daya daga cikin motocin malika ne sanda tana ganiyarta. Sai da suka iso gida kana Malika ta kira Saleem ta fada mishi isowarsu,azahirin gaskiya ya nuna murnan sosai,har saida sautin mirmishinsa ya Fito Fili,joda ko gyaran gidan tafara harda kichen sai da ta share ta goge datayi mganar girki ne malika tace tabari Mallam ya dawo don ita tunda tazo bata taba girki ba,Tunda bama iyawa tayi ba. Sun idar da sallar mangariba kenan sukaji hon din Shi megadi ya wangalemai get ya Shigo,jikin malika na rawa ta mike daga kan Darduma datake tana sakin Mirmishin jin dadi ga cikimta wanda yayi girma cikin doguwar rigar Material dake jikinta,da kallo joda ta bita,tana mamakin babu Abunda ke sanya Malika mirmishi sai Saleem Tun bayan rasuwar nan shine ganinshi ke sanyata mirmishi,kuma tafiyarshi ta sanyata kuka Joda bata gama mamaki ba,sai gashi yayi sallama bayan ya sawo kanshi cikin daki yana sanye da Uniform dinsa Harda hulanshi hannayenshi rike da manyan lodojin reasaurant har guda bayu,da malika yaci karo tana tsaye tana kallonshi cike da kewa,cogewa yayi yana binta da kallon Sha"awa baisan dalili ba,duk sanda yaga malika sai yaji yafi kowani Namiji sa'an mace mai kyau da tsarin jiki na mata. Yadda ya saki baki ne yana kallonta yabama Joda dariya,wanda tana ma gaisheshi bai ji ba,yana chan ya saki baki yana bin Malika da kallon sha"awa bata gama dariyan ba taga ya ijiye lodojin hannunshi asaman cafet din daki ya ware ma Malika hannu yana Fadin"Oya *YAR AMANATA..* Come here...'Yake fada yana sakin mata wani kayatattacen mirmishi. Itako kunya duk sai ya kamata ganin Joda tsaye,ganin taki zuwa ne yasa ya isa gareta da sassarfa ya Rumgumeta kam yana Fadin"Idanuwanki suna cike da kewata,ammh kinki ki Nunamin yadda kikayi kewata ko? Yafada yana tusa kanshi jikin Wuyanta Da hanzari joda ta bude kofa ta Fice tana yar dariya ita kadai. *Momyn ladingo..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *22* Malika taga Fitan Joda da sauri Abun sai ya bata dariya,ganin tana dariya ne yasa ya dagota yana kallonta Tunkafin yayi mgana Malika tace"Joda ce ta Fita da sauri.." Ido ya ware yana kallonta kafin ya kalli kofa yana Fadin"Wai dama ku biyu ne adakin nan..? Yafada kai tsaye yana shafa gemunsa,Dariya yabama malika sai da dan dara,Kumatunta ya shafa yana Fadin"Eh mana,dole na tambayan kinsan ke kadai nagani.."Mirmishi ta sakarmai kafin tace","Ai tama Fice Abunta,Sannu da zuwa.."Yana zama gefen gado yace"Yauwa ya hanya? kun dawo lafiya,ya karin hakurinmu..? Yake Fada yana rikota bai mata mazauni ako'ina ba sai akan cinyarsa,Yana zaunar da ita,Kanta na kasa ta zauna tana Fadin"Mungode Allah.."Kanta ya aza bisa faffadan kirjinsa yana Shafa kanta yake fadin"Allah yajikan Daddy da rahama yasa yana kyakyawan mtsayi.."Da Ameen ta amsa muryanta asanyaye Sun dade ahaka kafin ya tada ita zaune ledan Takeway din dayazo dashi ya dauko yana riko hannunta yake Fadin"Muje falo,na gaisa da joda,sai kuma naje nayi taking shower ko..?gyada mai kai tayi kafin ta rike hannunshi gam,su Fice daga Dakin yana rike da ita.... Joda na zaune suka Fito mikewa tayi tana dariya take kara gaishe da Saleem,ledojin hannunshi ya mika mata yana Fadin"Yauwa Hajiya Joda,barka da zuwa garin zamfarawa,Kiyi hakuri fa dazu ban ganki ba,kinsan Abunda akace amanace gareka toh dole sai ka kiyaye,kinsan Malika amana take awajena,shiyasa idona ya rufe bana ganin kowa sai ita.."Ba Joda kadai ba hatta malika sai da ta murmusa,karban ledan Joda tayi tana Fadin"Eh lalle naga alama,gaskiya acigaba da kularmana da Amanar Daddynmu muna son haka.."Tafada tana yar dariya Mirmishin yake yayi yana Fadin"Au kema kin bada goyon baya kenan,? Da hanzari Joda tace"Sosai ma.."Kada kai yayi kafin yace"Toh Allah bani ikon Kula da Amanar taku,ammh itama yar Amanar naku bata jin mgana,tacika taurin kai.."Yafada yana kallon Malika adage,hannu daya kuma yana Sosa dan sajensa,Dariya Joda tayi tana kallon Malika data shagala da kallon Saleem saboda yadda yayi mata kyau cikin Uniform dinsa na kakin yan sanda😂 Taimakama Malika yayi ta zauna bisa kujera kiss ya sakarmata a goshi kafin ya mike yana Fadin"Let me go and take Shower na dawo kinji..? Gyada mai kai tayi kafin tace"Toh..."bai kara mgana ba ya juya cikin takunsa na isa ya nufi dakinsa,daidai sanda wayarsa dake aljihu ta dau Tsuwan Neman agaji,Tana gani ya ciro wayar daga Aljihu yakara akunne daidai sanda yake Tura kofar dakinshi ya Shige tanajin sanda yake Furta"Amin Afuwa Madam.." Wani Yam taji acikin ranta,Nan da nan Zuciyarta suka raya mata abar sonshi ce Ta kirashi ma"ana amaryanshi,wani takukin abu takeji yana mata wayau bisa kirjinta,har sai da wasu siraran hawaye suka zobomata tayi hanzari sanya hannu ta share tana kokarin daidaita kanta,lokacin dataji sawun tafiyar Joda wacce ta Fito daga kichen dauke da Filet din data Juye musu abincin da Saleem ya taho musu dashi. Waina ce da miya sai Ferfesun kayan ciki,wanda shi din nema malika taci ba laifi tasha ruwa takoma tana maida Numfashi,itako Joda wainarta taci takoshi tanayi tana kallon katon talabijin dake Falon inda ake haska Shirin akushi da rufi daga Tashar Arewa24,tuwon Shinkafa ake koyawa nan da nan Joda tace"Anty malika gaskiya yakamata bayan kin haihu ki zage ki koyi girki ba dadi ace kullum ya Saleem na bisa hanyar Restaurant zuwa Siyo abinci alhalin kowa yasan yana da mata.." Tafada tana kallon Malika,wacce tayi zuru ta kurama Talabijin ido,Abunda Joda ta fada gaskiya itama tayi wannan Tunanin ammh rashin wanda zata fadamawa ne yasata tayi Shuru da bakinta,ammh Tunda har Joda tayi mgana bari tace wani abu,Cikin sanyinta na kullum tace"Tabbas hakane Joda na dade da wannan Tunanin araina,arayuwata na rasa abubuwa dadama daza"ace mace ta gari ta mallakesu,shiyasa Mallam zai kara aure.."Tafada tana Sharan kwallah,Ido waje Joda ke kallonta kafin tace"Wani mallam din..? Malika na kallonta tace"Saleem..."da hanzari Joda ta tsame hannunta daga Filet din wainar datakeci tace cikin tashin hankali.."Ki bari don Allah,? Wlh bansani ba yaushe zai yi auren? kuma wata yarinya ce..? Malika na Yamutsa fuskar takaichi tace"Karki ga laifinshi Joda wlh yayi kokarin sosai,samun Namijin da zai zauna dani Awannan zamanin wlh irinsu sunyi karanci,Bansan yaushe bane bikin ammh kamar Ummi tacemin wata uku akasa yanzu kuma da gayamin za'a kai wata Tunkafin rasuwar Daddy.."Tafada cikin rauni,Cak joda ta Dauki Filet din wainarta ta maida kichen taje ta wanko hannayenta tadawo falon kusa da Malika ta zauna tana Fadin"Anty Don Allah kidaina damuwa,Kinga Fa halin dakike ciki,kada kibari wannan mganar tasaki cikin damuwa.."Mirmishin yake Malika tayi kafin tace"Kinga na damu ne Joda? ni tsorona Daya yadda rayuwata zata dawo acikin gidan da zarar mallam ya samu nasarar auren wacce yakeso.."Zuru Joda tayi mata da ido kafin ta sanya hannu ta dafa kafadanta tana Fadin. ""Wlh bazaki Wulakanta ba Anty malika,haba aiko yadda yaya Saleem ke miki dagani yana cikin mayen sonki ne.."Idon Malika na maiko tace"uhmm haka kike gani dai,ammh babu soyayyata acikin ranshi sai dai tsausayi da kuma girmama girman Amanar da Daddy ya barmai.."Wani Shu'umin Mirmishi Joda tayi kafin tace"Haba Anty malika Kifa daina gaddama akan wai yaya saleem baya sonki...? Ai tsausayi shine ginshikin Soyayyaha,Tunda dai yana tsausayinki toh ina mai tabbatar miki da cewa yana Sonki har cikin ransa.."Tabe baki Malika tayi batayi mgana ba,sai ma ta yunkura ta mike tana mikama Joda Filet din Ferfesun kayan cikin data ke ci tana Fadin"Sakamin shi A fridge gobe da safe zanci.."Mikewa joda tayi tana Fadin"Toh Allah ya kaimu,ammh yakamata kima yaya Saleem mgana ayo cefene sai na dinga girkawa ni,ya huta yawon siyo abinci..". Malika na tafiya zuwa hanyar dakinta tace"Ki mai mgana mana.."Tafada cikin Kufula saboda harta Saleem din saboda kishi haushinsa takeji yanzu,Da kallon tsausayi Joda ta bita kafin ta kada kai zuwa kichen tana Fadin"Insha Allahu Anty malika zaki Farinciki arayuwarki,domin nima sai inda karfina ya kare na ganin kinyima sauran mata zarra agidan mazajensu. Shiko Saleem yana Shiga daki yafada gado suna cigaba da waya da zahra,wacce ke mai kukan Shagwaban Tun jiya ya manta da ita,shi dariya ma ta bashi,tana wani sangarta duk don ta burgeshi,shiko acikin ranshi yana Fadin"Duk sangartanki naga Malikata😂,ammh azahiri sai ya biyemata yana lallashinta da bata bakin tarinka hakuri dashi tasan yanayin aikinshi ko yayarta ta gidama hakuri take dashi Tunda tasan yanayin aikinshi,Zahra batasan dalili ba daya ambaci Malika sai taji ranta ya baci,ta alura akomai akace sai yace Malika kaza,abun na bata haushi Duk da ta riga tasan yadda badakalan aurensu ya faru,wanda abaya taso ta taso mai da mganar tana tambayanshi,Daure mata Fuska yayi yace kada ta sake tafara Shiga hurumin da ba nata ba,bayason rainin hankali sam,kuma a yarda ya nuna mata,bazai dauki ta raina mai malika,don zata samu matsala babba ma kuwa itako Zahra arawan kanta tagananin Malika bata da wani anfani wajen Saleem Tunda ya aureta ya saketa adaren Farko,sai daga baya ne ya dawo da ita,akwai ko ahaka tayi mata zarra😂🤔 Dakyar ta bari yashiga yayi wanka ya Fito bayan ya dauro alwala yazo yayi sallar issha'in data Subucemai,Shafa'i da Wuturin daya sabayi yau baiyi ba saboda nacin Zahra kawai biyemata yayi saboda sun kwana biyu basu wayar dare ba,koda Ranar ma sama sama suke mganar,Hira suke tasha tana bashi lbrin irin tanada tanadan datayima bikinsu wanda takejin kamar tajawo ranar biki zuwa gobe saboda Zumudi,Shi ko zumudin bayayi ammh ita datake budurwa rawan kafanta yayi yawa Shi har mamakinta yakeyi,tunda yake baitaba ganin Amarya mai Shigen rawan kafa ba irin Zahra,wanda halittace domin da zata bari data bari Tunda Momi na mata Fada,hakama Nadira wani lokacin kamar ta maketa takeji in tayi wani abun,shiyasa basa shiri da Yaya Nadir,saboda yadda bata komai cikin natsuwa..'lalle zahra kin samu mtsala😂 Bata barshi ba sai wajen 12 koda ya Fito Falo Tun har sun kashe komai na kayan Wuta sun Shige daki sun kwanta,bai shiga dakin ba ya dawo dakin yayi Shirin barci ya kwanta cike da Tunanin yadda zai Tunkari Malika da zencen kara aurenshi,bayaso yakara tadamata da hankali kan wanda take ciki,bata gama warwarewa,ammh ya yanke shawaran zai sanar da ita,ammh zuwa gaba kan lokaci ta dan saki ranta. ************* Washegari Da Saleem zai Fita office,Joda tayi mai mganar Cefane,hakika Saleem yaji dadi ko bakomai yanzu Duniya andaina kiwon Dabba kamar da,yanzu duniya cike take da masu saka ido,yanzu haka Allah kadai yasan mutanen da sukayi zundenshi na Siyan abincin dayake Tafe yi kullum ba ranar banza,Musamman yan wajen aikinsu yasan baza"a rasa masu dogon baki ba😂. Har afuska ya Nuna ma Joda jin dadinsa akwai yana Fita ba dadewa sai ga Sargent musa ya Kawo kayan Cefena niki niki,Joda ta karba ta kai kichen ta sanya komai cikin muhallinshi,da ta bude store din kichen din wanda ke shake da kayan abinci kala kala Nau'i Nau'i,nan da nan Joda ta zage damtse tana hada hadar Dora,girki ita kuma Malika tana daki yau ko Falo bata Fito yan mulkin sun motsa,shiyasa ko Saleem daya Shigo dubata da safe barci karya tayimai,har ya fice basu gaisa ba sai da ya Fita kana ta bude ido,tana bin bayanshi da kallo cike da Soyayyarsa mai Cike da muradi da sadaukarwa. Sai da Maman Abba ta Shigo kana Malika ta Fito da katon cikinta suka gaisa tana mata sannu,Joda ma dake kichen ta Fito suka gaisa kafin takoma ta cigaba da aikinta don Malika tace tayi mata Tuwon Shinkafa miyar Ganye,Maman Abba taji dadin ganin yadda Malika ta chanza ta cire damuwar komai acikin ranta,har ta nuna mata ta hanyar Furta mata,daga karshe tabata Shawaran ta rinka zuwa kichen din duk da haka tana kallon Abunda Joda keyi tana koya da haka zata sha mamakin abunda zata Tsinta kafin Allah ya sauketa lafiya,Malika taji dadin haka tace daman zaman kadaichi ya isheta in Joda ta Shige kichen ta barta ita kadai,gashi ita kallo bai dameta ba. Sai da Joda tagama Tuwon nan Maman Abba taci kuma tatafi dashi saboda yadda Tuwon yayi mata dadi,Malika ko taci taci takara kamar cikinta zai Fashe,wanda ya ragu Joda ta ijema Saleem,malika ta dauke tace shi zataci da daddare,dole Joda ta girkama Saleem farar Shinkafa da miyat kaji,Koda ya dawo Joda ta gabatar da abinci bakinshi ya kasa rufuwa nan Falon ya zauna dirshan yana cin abinci,ammh sai yaga Malika nacin Tuwo daya tambayi Joda ina Amanarshi ta samu Tuwo,nan take sanar dashi ita tayi dazu kuma yar Rigimar nasa ta dauke tace shi zata ci kafin ta kwanta. Kura ma malika ido yayi yana kallonta tana cin Tuwonta cike da Sanyinta yadda ta saba,mirmishi kawai yayi yana Fadin',Tunda itace zataci toh nayi mata afuwa,ammh da wani ne yau Allah bazan barmai ba.."Yafada yana Hade giransa waje daya Dariya joda ta dinga musu tana Fadin"Kunfi kusa aie..In ma zaka karbi kayanka ne babu Ruwan Joda aciki.."Yana cin abinsa bai sake mgana ba,saboda yaga yau din Mulkin Malikar ya motsa ne,ganin haka yasa joda ta Shige daki ta barsu anan. Shima yana kammallah jin abincin da kanshi ya kwashe kololin zuwa kichen ya wanke hannayenshi ya dawo Falon yana kallon Malika tana wani yamutsa baki,gabanta ya karisa yana kallonta kafin yace"Ya..? kin koshi ne..? Kai ta gyada mai akarkace,Filet din Tuwon ya dauke ya nufi kichen dashi da sauri tace"Don Allah asamin a fridge gobe zan karya dashi.."bai juyo ba,kuma bai yi mgana ba ya Shiga kichen din yasanya mata shi cikin Fridge din ya Fito. Yana zuwa gabanta baiyi wata wata taji ya daga cak,ya sakata cikin kirjinsa da ita,kuri tayi mai da ido tana binshi da kallo ganin hanyar dakinshi ya dosa da ita,shiyasa tace"Ban wanke hannu ba Mallam.."Bai mata mgana ba sai da ya direta bisa gadonshi kafin ya durkusa kusa da ita ya Dauki hannun damanta wanda taci tuwon dashi ya saka abakinshi yara lasheshi daya bayan daya,sai da ya sule hannun tas,yana yi yana kallon kwayan idanuwanta,Lumshe ido take tana jin wani yanayi yana Shiga jikinta. Sai da yagama lashe hannun kafin ya mike yana kallonta yace"Daga yau kinga makwancinki nan,ke ko kunyar Joda bakiyi ga dakin mijinki ammh kina kwana da wata katuwar mace.."Yafada yana Shafa gemunsa daya Tsirowa na rashin kunya😂,Ware ido tayi tana kallonshi kafin ma ta samu zarafin mgana ya Fada tiolet yayi wanka ya wanke baki kafin ya dauro alwala koda ya Fito jikinsa babu riga,sai dogon wandonshi Jikinsa gabadaya yana digan Ruwa,jallabiyansa ya sanya ya shimfida sallaya ya tada sallar Shafa'i da Wututri yayi kafin ya rufe a addu'o,insa,Koda ya idar da Sallan Malika ta dade da yi barci,shiyasa yana tashi ya dauketa yakaita tsakiyar gadon ya gyara mata kwanciya,shima cire jallabiyan yayi da dogon wandon jikinsa,Ya bar kanshi daga shi sai gajeron wando ya Kwanta kusa da Malika ya Rumgumota kam,yana sakin ajiyar Zuciya,itama cikin barci ta zagaye hannayenta bisa cikinsa ta rikeshi gam,Blanket ya Rufa musu yana shafa maran Malika zuwa saman Tulelen cikinsa haka kurum yakejin Nishadi na Shigansa,yana jin wayarsa na Dukan neman agaji ammh ya share don yasan zahra ce,shi haushin datake bashi ta manta yana da mata ne? ammh sai ta dinga kiranshi duk sanda taga dama,Tsaki yaja aransa yana Fadin dole ya tashi tsaye don ya lura sam zahra bata da adalci. ***************** Kwanaki suna ta gangarawa ayayinda muketa cinye kwanakinmu Aduniya,Ahaka ne har gashi auren Zahra da Saleem yana ta matsowa har yarage saura 4weeks ta kowani bangare anata Shirye shirye musamman ma bangaren uwar gayyah zahra,tun akwanakin da suka rage tafara banke banken mganugunar mata kamar hauka,wannan kuma shawarar Nadira ce itace kan gaba wajen amsomata tana duramata ammh basu bar momi tagani ba don susan zasu ci ubansu. Ta bangaren Saleem ko baya wani Shirye Shirye domin ayanzu yafi jin dadin rayuwarsa Fiye data kullum,Domin shakuwa mai cike da salon soyayya ta shiga tsakanin Malika da Saleem,wanda shi Saleem din bai Fahimci haka ba,Sakamakon zuwan Joda shi yakara musu kusanci da juna,shine sanadin kwanansu waje daya wanda yayi sanadiyar kara musu Shakuwa da kusantan Juna. Duk da halin da malika ke ciki da zarar Saleem ya nemeta bata iya mai gaddama zata bashi dukkan Hadin kai da zai samu natsuwa,shikuma yana son binta ahankali saboda cikin jikinta ammh kuma zumarta ne ke janshi wanda indai zata kwana cikin jikinsa bai ya kauda ido akanta sai ya lalubeta ko kadan ne,ita kuma bata iyamai gaddama,domin yakoya mata jarabanshi bata iya hakuri dashi indai yana nan tana kakume dashi. Daga bangarenshi babu Shirye shiryen dayake gudanarwa ko kudin kayan aure ma Ummi ya tura kudi a banki ta bada oder kayan akwatuna,tsarin Shirye shiryen bangaren amarya kuwa sai da ya bude musu Wuta ita da Nadira,Abun takaichi aure kamar wani auren Mawaki,Evets wajen goma suka lissafomai baki ya sake yana kallonsu daga karshe ya Rufe bakinsu da Fadin Shidai banda daurin aure babu Abunda zai hallata,so in ma sun Shirya bidi'o'insu toh shi dai bandashi ayi lafiya 3hundered thausand ya tura musu yace suyi Abunda ya zama dole,sai kuma yahadasu da Sadiq tunda yaga yamatsamai Shiyasa ya hadasu don yaga shima dan Rawan kan ne kamar su. Baita yarda yayi ma malika mganar ba,itama batayimai ba,sai ranar Suna kwance bayan sungama Samun Natsuwa tana kwance bisa kirjinsa,wayar Saleem tayi ta daukan daukin kira,wanda lokacin after 11 na dare ne,yana ji ammh sai ya dauki wayar ya kashe,ganin haka yasa Malika cewa"Ka daga kiran ka Mallaam.."Tafada cikin karfin hali. Yana jinta yayi mata Shuru ammh kuma yana Rumgume da ita yana Shafa gashin kanta zuwa bayanta,Cikin kasalattaciyar murya yace"In dauka fa kikace?kinsan waye ke kiran ne..?Kai tsaye tace"Na sani ba amaryanka bane.."Abazata yaji mganar nata,duk ya ji wani iri ammh sai ya dake cikin karfi hali yace"Waya fadamiki zan kara aure.."Kai tsaye tace"Ummi ta sanar dani tun lokacin da aka sanya ranar.." Shuru yayi bai kara mgana ba,itama sai taja bakinta ta tsuke,still kuma Zahran bata hakura ta daina kira ba,afusace ya dauki wayar ya kasheta gabadaya yana tsaki cikin ranshi,har ta Fidda rai da zai mata mgana taji yace"Ammh meyasa baki taba Nuna min Ummi ta sanar dake ba.."Tana kwance bisa kirjinsa bata dago ba tace"Saboda baka bani damar haka ba,bansani ba ko kana Tunanin cewa zan hanaka kara aure ne,nikuma ko daya babu yarda zan ce ka zauna dani ni daya mallam,Allah yabada zaman lafiya yasa ayi sha'ani lafiya agama.."takarishe Fada tana Sharan kwallah. Tsausayinta ya kamashi,Fuskarta ya dago yana Share mata hawaye yake Fadin"will tok later,juz sleep now kinji..",Gyada mai kai kawai tayi takoma bisa kirjinsa ta lafe,shikuma yana ta lallashinta ta hanyar Shafa bayanta zuwa kugunta cike da salon lallashi,har barci ya kwasheta shiko idanuwansa biyu yana Tunanin yadda yanayin zamansu zai kasance irin zahra ta Shigo rayuwarsu. *************** Bai kara tada mata da mganar ba,shiyasa itama tayi mai Shuru,bata karamai mganar ba sai da taga yafara gyaran gidan,gabadaya dakunansu zuwa falon duk an chanza komai da komai anyi sabon Fenti,kuma daga yammah daga Falon ya Fitar da dakinsa,aka gyara aka zuba komai da Malika taga haka sai tamai mganan cewa badai anan zai saka amarya ba,sai ya bata amsa da cewa eh anan gidan zata zauna,ammh adakinsa,shi kuma Zai koma sabon dakin daya gyara,sai Malika tace Me zai hana su koma gidan da Daddy ya bashi su zauna dukkansu,sai ya dinga zuwa musu Weeked. Ya dade yana kallonta cike da mamaki kafin ya girgiza yace mata"Bazai yuyu ba,bai zauna da ita acikin gidan da akabashi saboda ita ba,cin Fuska ne wannan kawai ta barshi tazo nan su zauna,kuma Shi baya ra"ayin zama shi kadai yafison ya hadashi matanshi waje daya ta bari in tana so ta zauna agidan ta bari sai ta haihu sai su rinka zuwa suna hutunsu achan,data mtsamai sai ya bata Fuska yace tadaina ma Damunshi Dole Abunda ya tsara shi za"ayi. *************** Biki saura Sati biyu Aka kai akwatunan aure kano,wanda Ummi da ita da wata kawarta da wasu goggonin Saleem yan kumo suka kai kayan,akwati takwas,shake da kayan arziki wanda aka karbesu hannun bibbiyu Abunda sai wanda yagani,Suma achan din anyi musu kara sosai sunci sun sha,kuma sunyi guzurin Abun soye soyen da'akayi musu basu ci ba,Takwaichin Turaman atamfafi ashirin Hajiya Saratu momi ta basu da kudi 50k,Daga kano zamfara suka Wuce suka kaima Malika kayanta wanda aka hadamata dana Haihuwa,Dayake tayi scanning ance mace zata haifa,akwati hudu nata uku kuma kayan bbys ne Abun sai wanda yagani,Malika taji dadin zuwansu ba kadan,ita da ada take jin haushin baki suzo gidansu,ammh sai gashi yau Malika tana neman ma bako yazo wajenta koda daga kauye ne.. Ba Aranar suka koma ba,sai washegari suka koma Abuja,wanda kafin tafiyarsu sai da suka tara Saleem da Malika suka yi musu nasihan da fatan su xauna lafiya da junansu,Amarya kuma Ummi tace ranar da za'a dauko ta daga kano Abuja za"a kawota sai ta kwana kana washegari su wuto zamfara da ita. *momyn ladingo..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *23*   Abangaren gidansu Zahra ne Shirye Shiryen yafi yawa saboda itace uwar gayyah,Tun ana saura sati daya biki Hajiya Saratu momi ta dauko hayar wata Falmata mai gyara amare daga maiduguri,wacce zata gyara Zahra ciki da bai kafin ranar bikin yazo,Hakika bakaramin burgeta momi tayi ba,haka takasa boye murnata afili dama ita burinta taje ta rikita Saleem wanda zai manta da kowa da komai sai ita shalele Fatimatul zahra'u. Bangaren gidansu Saleem kuwa Abbi shima ya saki aljihu ana ta Shiryen shiryen biki,Tunda daga kano Abuja za'a kawo zahra sai ta kwana washegari su Wuto zamfara da ita,wannan Auren na musamman ne,domin yazoma Saleema akan gaba,sun gama Final Exams dinsu ta tararro ta dawo gida aka Shiga shagali da ita tayi alqawari sai ta chusama Malika haushi Sosai da sosai,Balle ma Da Sadiq ya sanar da ita itama Zahran ba baya ba akwai kyau ga iya kwalliya da Iya tsara kalamai,Kawai sai taji lokaci ta burgeta saboda neman suna harda karban nombarta ta kirata suka gaisa. Itako Zahra an samu nayi ai sai aka zare an samu kanwar miji abagas,abun takaichi ma Saleema bataji kunya sanar da Zahra duka sirranka auren Saleem da Malika wanda batasan dasu ba,yazamana Family issues ne,itako zahra kanta ya fashe harda daukan ma Saleema alqawarin sai inda karfinta yakare game da mallakan Saleem,harda ikirarin sai malika ta barmata gidan🤔.,Saboda munafuncinsu yazo daya,sai ga Saleema ta Shirya kayanta tsab tatafi kano gidansu zahra tace chan biki zai fi dadi,Allah barshi in Za"a kawota sai ta biyosu su dawo tare,Ummi da Abbi basu zargi komai ba sun zata dama kila chan kawayene suna da kyakyawan alaqa duba da itama Saleema zamanta yafi yawa akano,basu san ko kullewan ta munafunci bane. Duk wannan Abun Saleem bai san dashi ba don babu wanda ya sanar dashi,Dayake ma Saleema yanzu bata gabanshi Tunda sukayi karon nan da ita agida yadaina mata dariya,gabda bikin yaga kiranta ammh sai ya Shareta bai daga kiran ba kuma bai calling dinta back,sai ana gobe biki yana Shirin tahowa Abuja inda zasu hadu anan gidan Abbi su Tafi daurin Aure,Zahra ta kirashi tana rokonshi don Allah ya iso kano yau ya hallarci Dinner dasuka Shirya,kawai sai yaji kamar muryan Saleema cike da mamaki yake tambayan Zahra murya wa yakeji kamarta kanwarsa Saleema..?Zahra na mirmishi ta sanar dashi itace,gabansa ya fadi hannunsa bisa bakinsa,yana jinjina al"amarin na Saleema tsoro ya darsu ranshi rai bace yace zahra tabata waya nan akaba Saleema waya ta karba tana gaisheshi bai iya amsa gaisuwanta ba ya kira sunanta a kakkaushe..    "Saleema,Don ubanki uban me kikazo yi gidan su Zahra..? Tana tabe baki tace"Yo laifi ne don nazo gidansu matar da zaka aura,Don mutaru muyi shagalin biki tare..? yana Numfarfashi ya tare ta yana Fadin"Ke rufemin baki munafuka,kinsan Allah Saleema kinsan dai nasan halinki wlh tallahi in naji wata mgana ta Fito to nasan daga bakinki ne,Kuma sai naci ubanki na kakakkrya ki shegiya Mai dogon baki kawai.."Yafada yana huci ya yanke kiran,Tabe baki Saleema tayi kafin tace acikin ranta"Ni ba munafuka bace.."Tafada tana murguda baki kamar tana gabanshi,Nadira ce ke tambayanta ko lafiya,sai ta barsa tace bakomai..," Abangaren Malika ma,Joda da Maman Abba suna ta gudanar da Shiryen Shiryen zuwa amarya ta ango,Maman Abba da kanta ta karbi kayan Malika wajen kala biyar taba telanta ya tsaro mata dinkuna na gani na fada,kuma saleem yabada kudin da kanshi,kuma zahirin batu dinki sun Fita sosai,Gashi yayi mata masu yalwar saboda cikin jikinta. Duk da Malika na boye kishinta bata bayyanashi ammh yau kam takasa control din kanta,balle dataga Saleem ya Shirya kayansa Zai Wuce Abuja bazai dawo ba sai jibi in sun taho da amarya,tana zaune agefen gado sanye da doguwar rigar Atamfa cikin dunkunan da Maman Abba ta dinkomata,tayi mata kyau sosai balle da cikinta yakara tsufa,sai ta dan kumbura kadan fuskarta ta cika sai takara kyau,tagumi ta zabga hannu biyu tana kallonshi yana kokarin saka botir din gaban wani yadinsa Fari ammh Shara shara ne,domin hatta Farar vest dinsa ana gani,Hulansa ya dauko xanna bukar,mai adon baki ajiki domin aikin jikin rigar baki ne,Yadorata akai agogonsa baki na fatar damisa yake daurawa kafin hankalinsa ya koma kan Malika wacce idanuwanta suka fara cika da kwallah. Yadade yana kallonta kafin ya saki ajiyar zuciya ya karisa kusa da ita,har ya durkusa gabanta bata Sani ba,sai da sanya hannu ya ciremata hannuwan datayi tagumin dasu,kana ta dago tana kallonshi ido cikin ido, Kwabe Fuska yayi yana kallonta yace"Why...? Haba Amanata meyesa kikeson Allah ya kamani ne? ehe kina tagumi abunda kikasan babu kyau meyasa kikeyi..? Ajiyar zuciya ta sauke tana kallonshi dukar da kai tayi saboda bazata jure kallon kwayan idonshi saboda suna dauke da wasu sirranka wanda suke haddasamata wasu irin yanayi atare da ita. Kanta na kasa tace"Na daina.."Ta fada tana sosa hanci dan mirmishi yayi kafin ya saka hannu ya dago habarta yana Fadin"Mejego..Uhmmm..Menene fadamin naji..? Yafada yana shafa lebenta da hannunshi guda daya,rikemai hannu tayi tana kokarin maida kwailarta tace"Katashi katafi kada kayi dare a hanya..",Kwayan idonta yake son gani,ammh sai taki ta rinka kauda kai,shikuma yana binta da ido,ganin haka yasa yatashi tsaye yasa hannu ya dagata tsaye yana Kallonta cike da kulawa,bai bata zarafin mgana ba, ya budemata hannuwanta tafada,lokaci daya ta saki kukan data ke rikewa Tun dazu.."matseta yayi yana shinshinar Wuyarta cike da salo,lokaci daya yana Shafa cikin jikinta,Tunda dama ta gefe ya Rumgumeta,saboda cikin daya yi mishi shamaki. Sai da tayi kukanta ya isheta kana tayi Shuru tana Ajiyar Zuciya,tare da sauke Numfashi,Mirmishi yayi yana Kara gyara mata daurin dankwalinta bayan ya bata Sumbata asaman tsakar kanta yake fadin"Kamar kada natafi Amanata,inaji ajikina zanyi kewarki sosai.."Da sauri ta dago kanta tana kallonshi kafin tace cikin sauri"are u Sure zaka yi kewata mallam..? Yana kallon cikin kwayan idanuwanta yace"Very Sure..Kefa zaki kewata..?Bata iya bashi amsa ba,sai kawai tayi dage ta kama lebenshi tana tsotsa da sauri rike kanta da hannu daya yayi,hannu daya kuma yakara mtseta cikin maranshi cike da salo Malika take sumbatarshi har sai da suka gaji kama suka saki juna suna maida numfashi,bisa kirjinsa ta lafe tana Fadin"Zanyi kewarka sau ba adadi mallam,kariga ka zama jinin jikina,rayuwata bazata iya tafiya ba sai da kai,ina nace maka bani son zama dakai akoda yaushe wlh nayi karya mallam,i so much luv u,don Allah karka bani ko bayan kayi aure.."Tafada hawaye na wanke mata Fuska.    Wani sanyi yaji ya Shiga cikin ransa,cike da farinciki ya damki Fuskarta da hannu biyu yana kallonta yace"Da gaske kina sona malika.."?Gyada mai kai tayi hawaye suna kwaranyomata,Bakinta ya sumbata kafin yace"Duk da yadda na lalata rayuwarki na toxartaki keda mahaifinki..? Hannayenshi ta damke tana Fadin"Da shine ma nakejin ka mamaye duka raina,kayi sanadiyar Chanza malika zuwa wata malikar dabam,in ko hakane ka taka muhimman rawa arayuwata mallam,ka koyar dani abubuwa dama,wanda ni banda bakin godemaka sai dai nayita maka addu"an Allah ya saka maka da gidan aljannah Firdausi.." Bai samu zarafin mgana ba,illah matseta dayayi ajikinsa yana shakan kamshin Turarenta,cikin wata murya yake fadin"kinsa me? bai bata zarafin mgana ba ya cigaba da cewa"Nima sai daga baya nadinga jin Abunda na aikata gareki ban kyauta ba,mussama ranar danaje daukanki agidanku naji matukar kunyar yadda Daddy ya karbeni batare da yayi Duba da irin Tozarcin dana miki ba ya karbeni hannu bibbiyu kuma wani karin nadamar tawa yadda yabani ke batare da Gaddama ba,ranar naji kunya sosai.."Mirmishi tayi kafin tace"Ni kuma abu daya ke ban haushi a abunda kayi min in na tuna..? Dago kanta yayi yana Fadin"Menene shi..? Gira ta matse tana Fadin"Har ka manta.."Tafada tana hararanshi,ware ido yayi kafin yace"Srry gayamin don Allah.."Yafada yana Shafa dogon hancinta zuwa karamin bakinta,Shagwabe Fuska tayi kafin tace"Yadda ka karbi Virginity na da karfin Tsiya mana.."Tafada tana Wulkamai ido cike da salo,Mirmishi ne ya Subucemai wanda sai da duka fararen hakoransa suka bayyana awaje,hannunta ya riko yana Shafawa har zuwa saman kirjinta yana mirmishi kafin ya gangaro zuwa katon cikinta,cikin husky voice yace"Ni kinga wannan daren D Unforgtable Night and moment kenan bazan taba manta wannan Daren ba.."Yafada yana Shafa cikinta yana wani munafikin dariya. Fuska ta kwabe tana kallonshi kafin tace"Saboda mene...? Hannunsa ya dora bisa lebenta yana zagaya babban yatsanshi dashi yace"Baki sani ba..? ta gyada kai tana kallonshi Yar dariya yayi kafin yace"Dare ne mai cike da Tarihi ,dare ne da kika Shayar dani wata zuma mai dadi wanda banta zaton akwaita ba,Wlh tallahi i can Explain buh abu daya na sani ke ta dabamce domin Haryanzu kina kan Shayar dani wannan zumar,sai dai na ranar is so Sweet and special.."Yafada yana kanne mata ido daya,Dariya da kunya suka kamata,sai takaimai duka Kirji tana mai kukan Shagwaba dariya yake yana Fadin"Allah am Serious,ko zaki karamin ne,sai na kara tabbatarwa.."Wata uwar harara ta makamai kafin ta warci hannunta tana kallonshi,Juyawa tayi ta dauki yar jakarsa wacce ya sanya kaya ta rataya tana Fadin"Ni..? ai yanzu mun tsufa abari amarya tazo sai tabaka sabuwar zumar,muje na takamaka kaga dare nayi kuma,sadiq karya ga kamar ni na tsaidaka.." Yana dariyanshi na Nishadi yabiyo bayanta tana tafe da kyar yace"Ai wlh kece kika tsaidani ko ya tambayeni haka zancemai,mganar zumar amarya kuma nidai Taki nasani ki bari in tazo na dandani tata,sai na tantance.."Yafada yana shafa gemunsa na rashin kunya cike da Nishadi tana jinsa tayimai banza ta Fito daga dakin tana mirmishi cikin ranta. Har cikin kichen din yabi Su maman Abba yayi musu sallama,sukai mai fatan isa lafiya,da kuma Fatan Allah yasa adaura aure lafiya,Tare suka Fito da malika har haraban gidan ita da kanta budemai mota ta turashi,saboda taga bai da niyyar Tafiya sai kwakwumarta yake jakar kayansa ta sakamai akujera mai zaman banza kafin Tarufe mai kofar mota taja gefe tana dagamai hannu,Jagale yayi yana kallonta kafin ya bude murfin motan ya Fito,kawai sai ji tayi ya Rumgumeta kam kam,yana Sumbatar wuyanta,itama matseshi tayi tana kokarin maida kwallarta Sai da suka dau tsawon lokaci kafin ya saketa yana Riko hannunta yace"Ki saka ashafa miki wannan jan Abun na mata,zai yi kyau da hannunki.."Bata kalleshi ba tace"Toh.."Yana kallon Fuskarta yace"Kinji..Don Allah kiyi ko don ni kinji Amanata.."Muryanta cikin sanyi tace"Zanyi insha Allahu.."Mirmishi ya saki kafin ya duka ya Sumbaci bakinta,yana dagamata hannu ya fada mota,ya daura Set belt ya tada motan yana kallonta tana dagamai hannu,shima dagamata yayi kafin yayi Riverse da motar yazuba hon megadi yataso da sauri ya wangalemai get ya sulala waje Malika ta dagamai hannu,sai da ya karisa Ficewa megadi ya maida get ya Rufe kana ta juya zuwa cikin gidan tana Share kwallar data zubo mata. Tana shigowa sai ta Wuce dakinta tashige tiolet taci kukanta kafin ta wanko Fuskarta ta Fito,cikin kichen din tabi su Maman Abba,wadanda ke ta aikin soye soyen miya da naman kaji bakin da zasu yan kawo amarya Tunda su ba taro zasuyi ba,Abunda yayima malika dadi da Hajiya binta ta mata waya tace Goggon daga malumfashi, da Wata zaliha wacce take ya ga Daddy zasu zo mata gobe,Ho zo kuga murna har bakinta yaki Rufuwa ko bakomai ashe dangi ma suna da ranarsu,gashi zasu suyi mata rana lalle duk wanda baisan darajan dan adam ba,yana tare da Nadama duniya da lahira. Nan take tambayan joda wani abu ne ake sanya ma Hannu yayi ja,Mallam yace tasaka,Maman Abba da joda suka sanya dariya harda tafawa,Joda ne tace"La Anty Malika Kunshi fa yake nufi.."Maman Abba ta karbe da cewa"sha kuruminki dama nayi ma wata Mami mai lalli na kusa damu mgaba tana kitso tana kunshi,so gobe zan kawota tazo ta Chanchare min ke,yadda Acp zai ka rikice yakasa gane Amarya da uwargida.."Dukkansu suka sanya dariya suna cigaba da aikinsu suna hira ita kuma malika na zaune tana tayasu da hira,gefe daya kuma tana sakin mirmishi ita kadai.   ***************** Koda Saleem ya isa Abuja ya tarar da gida cike da Yan"uwansu wadanda suka zo daga kumo,maza da mata,wadanda zasu tafi daurin aure gobe,Koda yaje Sadiq ya gaji da jiransa har yayi Fushi ko takanshi baibi ba,saboda haushin dayake bashi na yadda yake wani rawan kafa,akan aure,Abun takaichi ma sai mutum yaga yadda Su Nadira suka maidashi kamar wani kakansu komai suke so shi suke kira suna rawan kafa gayamusu shi kuma yana rawan baki sanar dashi,harda mai masifan kin zuwa da Wuri su wuce kano ayau su samu Dinner dasu Zahra suka Shirya,wani dogon tsaki yajama Sadiq bai kara tankanshi ba,ya Cigaba da laluban nombar wayar Malika yana so ya sanar da ita Ya iso lafiya.   Abokan wasansu kuwa sai tsiya suke mai,suna fadin yayi rawan kafa,da Son mata ko kuma suce mai jaraba ne,Akanannan Shekararunsa har yatara mata biyu,Dariya kawai yake musu yana Fadin"Kunga alamun cewa Saleem lafiyayye ne,don da bani da karfin mazantaka da ba'a kara bani wata matar.."Rufe baki sukayi suna sunne kai sunji mganar dayafi karfinsu,Dariyan mugunta yakeyi cikin ranshi,dama da gangan yayi saboda ya kashe bakinsu.    Ya marwan kuwa da bai samu zuwa ba,ya taimaki kanshi don haka suka tasa mai tsiyan yaki aure har kaninshi yana Shirin yin na biyu raggo kawai har suna Fadin in bai lahiya ne ya sanar su neman mai mgani,dariya takama Sadiq yayi ta darawa har sai da yakira Marwan din yabashi lbrin,dariya yayi kafin yace"Kamar yasan za'a rina,shiyasa ya noke wannan karon,ammh shima insha Allah da zarar yahadu da wacce yakeso zai yunkuro.."    ****************** Washegari da karfe 11:30 na Safe aka daura Auren *SALEEM KABIR KUMO* Da Amaryanshi *ZAHRA BUKAR MADA* akan sadaki mafi daraja Dubu Dari da hamsin,wanda aka daura akofar gidan Alkalin Alkalai bukar mada,daurin auren daya samu hallarta kusoshin gwannati dadama wanda sai dai wasu ka gansu acikin jarida ko gidan talabijin. Bayan gama Daura auren aka Shiga gaggaisawa,musamman Abbi wanda yake ta sallaman jama'a wadanda suka zo dominshi,shiko angon Amaarya yana gefe,sanye da wata Navy blue din Shadda wacce taji aiki,riga da wando har da babban Riga,sai hulanshi zannah bukar,Shida Sadiq suka sha anko wanda Sadiq din ya Siya shaddan ya kuma dinka musu suka sanya,Sadiq ne keta hada hadar jam'a bakinshi yaki Rufuwa ammh banda Saleem,wanda ya wani hade rau,in kaga yayi dariyan yake toh anzo an bashi hannu ne,ana tayashi murna da Allah sanya alheri. Su Abbi basu Wuce ba,sai da Bukar mada yatsayar dasu sukayi walima acikin babbann falon gidanshi,wanda sukaci suka sha,suka tashi suna fatan Allah yabada zaman lafiya,Suko su Saleem da sauran abokanshi basu bi tawagar su Abbi su zasu tsaya su taho da amarya..       Tun after 1 Saleem ke masifan Yakamata su Fito su dau hanya,saboda kada suyi dare,don shi yagaji da jira,ammh kuma tawagar amarya suka ki fitowa,Dole tasa Sadiq yajasu da sauran abokan aikinshi zuwa cikin gidansu Zahra suka gaida iyaye da baki,Amarya suna wani bangaren na gidan,sukaji lbrin Shigowar ango cikin gidan,ai zahra dake zaune ana gyara mata Fuska wacce aka Firgita Fuskarta da kwalliya kamar wata aljanna,tana sanye da wani leshi dinki riga da sikat,wanda ya Fito da Suran jikinta,saboda yadda kayan suka kamata,bata ma jira sauran kawaye ba,ta fito Mayafi ahannu,su Nadira ne suka biyo ta da gudu da jakarta suna kokarin gyara mata mayafi. Lokacin da Saleem yaci karo da Zahra da farko ya tsorata da Fuskarta ganin yadda aka chabamata abubuwa babu kyan gani,kamar wata aljannah,Abunda yafi bashi mamaki babu kunyar Amaren zamani afalon gidansu gaban dubban jama'a ta rikoshi tana mai mgana cike da shagwaba,Sagale yayi mata ammh kuma ya chanza Annurin Fuskarshi kwata kwata ya tsani mace mara aji da kamun kai,shi Tunda kan malika yadaina ma mata kallon goro,toh ji dai malika bai taba zata zai sameta aburduwa ba,ammh sai gashi ta bashi mamaki,Ammh kalli zahra Da yake ganin tatashi cikin hausawa ammh ji Abunda take kamar ba diyar hausa Fulani ba. Haka ta matsamai suka yi hotuna tana manne dashi,Kawayenta ma duk sunyi hotuna da Sauran abokanshi,Saleema ma tashigo sunyi hoto,ammh fa yanayi yana hararanta,saboda haushinta yakeji,ganin yadda ake Kiranta ko'ina kyace gidan ubanta ne,ko wata kanwar uwarta,Chan suka ja gefe da Sadiq suna gulmansu na fama yana kallonsu aranshi yace"Munafukai kawai... Suna gama hotuna aka zo aka ja Zahra aka kaita wajen Babanta yayi mata nasiha daganan sai dakin Hajiya saratu momi,itama tayi mata nasiha daidai gwargwardo,acikin nasihan nata taja kunnanta kan ta rage rawan kan nan nata,da shigen Fi'ili da kuma tsiwarta,don wasu mazan basu son Rawan kai,daga karshe ta mata Fadan tabi mijinta,ta kuma zauna da abokiyar zamanta lafiya,kada taji wani baraka ya bullo daga barayinta,Zahra na dunkunkune cikin mayafi kamar ta Allah nan ko Allah Allah take  asadata cikin mota don Nasihar Momi ba Shiganta yake ba,Cikin ranta fadi take"Kishiyar ne zan bi ? Hala ita ta auroni tabdijam ai kowa tashi ta Fisshine.."Take fada babu ko alamun Nasihan ya Shigeta. Haka aka Fito da zahra,ko hawaye babu a idonta,koda na gulmar da amaren zamani keyi ita batayi ba,idonta kir,sai da Nadira ta maketa ta ja mayafinta ta Rufe mata Fuska tana mata mgana cikin kunne kana ta daina Fito da kanta waje😂,Motoci hudu ne suka tafi Abuja,Domin bukar mada yace bayason bidi'an nan duk maison zuwa daga baya yaje ganin daki,duk da dama ango yace amayar kadai yake bukata basai an kawomai wani kaya ba,toh dayake Duniya tana cike da yan boko da masu dashi,shiyasa suma iyayenta basu damu ba. Motar Sadiq aka sanya amarya Saleem Tun da yaga ana bata lokaci yabi motar wani abokinshi Dcp Sulaiman gidado(Na kishin mata),kusan dama abokai ne😂 ,kuma halinsu yazo daya suna da Shigen jinkai da rainin wayau,suka kamo hanyar Abuja su biyu suna tafe hiransu ta abokai suna Shekewa da dariya,shi gidado shi kebama Saleem wasu dabarun zama da mata biyu,saboda shi yariga yin gaba,Hafsa da Jameela suna fafatawa dashi,duk ya da tara daya gida har yana ba Saleem shawaran duk wacce ta kawo wargi ya bata takarda ya sanda ta gida😂   Dangin mamanta biyu sai na babanta daya,sai kawayenta biyu sai Nadira da Saleema sai zahra su kenan,Suka kamo hanyar Abuja,Zahra tana ji kamar ta bude ido taga sun isa,don ma Nadira ta kwabeta da farko tafara gaddama bazata Shiga motar kowa ba,sai ta angonta wanda tuni yakara gaba,kujimin Amaryar zamani gaakiya Zahra zamanki cikin gidan Saleem akwai shan kallo..."!. **************** Sai bayan mangariba suka iso gidansu Saleem,nan fa kallo yakoma sama domin ganin tsaruwa na gidansu Saleem,zahra tana cikin mayafi ammh tana kokarin Fito da kai,sai da Nadira ta damketa dakyau tana mata Fada,Ummi da kanta ita da kawayenta suka Fito suka tarbi amarya da yan'uwanta cike da Farinciki da murna,suka dumguma zuwa cikin gidan inda akayi musu masauki adakin na mussaman da'a gyara domin su. Nan da nan Aka fara jera musu abincin da ababan Sha da'aka tanadar domin su,wasun su ne suka fara gudanar da sallar kafin sufara cin abinci,ammh irinsu Saleema da Nadira sai da sukaci suyi nat,Abunda zai baka mamaki sai ganin Zahra ta cire dankwali ta Cire sikat tana zaune daga ita sai rigan Leshin jikinta da Underwears,ta Iyayen ciki suka mata mgana sai tace,zafi takeji bazata iya zama da Sikat din ba,Ai nan gidan iyayen mijinta ne,So kamar gidan Mijinta ne,Rike baki kadai sukayi suna mamakinta,basu gama mamaki ba sai gashi ta Fito da wani hadin gumbar mata tanaji,Duk kyafta mata idon Nadira keyi saboda Saleema awajen bata gane ba,Da wata kanwar Babanta ta mata mgana sai takara narke Fuska tace'Yo ni goggo Shatu,in bantashi tsaye na taimaki kaina ba,kawai sai na zauna tunda dai kun kasa,ai ni sai nayi Tunda gidan kishiya zan Shiga abun sai da tanadi.." Tafada hankalinta kwance,daganan ba wacce ta sake mata mgana,Kowacce ta kama kanta,tunda sunsanta bata da kunya ko kadan,Itako zahra harda tafawa da Saleema tana kara zugata,Nadira dai Shuru tayi tana tsoron kada Zahra ta tafka kuskure,koda wani abu ya bullo Saleema yar"uwanshi ce, bazai taba rabuwa da ita,itafa Yana da ikon da zai yarda kwallan mangwaro ya Huta da guda..." . _Yan gidan *MALIKA MALIK PAID GROUP* Kuna sha'aninku kucigaba da gashi Suya sai ranar da Saleem ango zai Shiga dakin Zahra'u Amarya😂😛😜😱😹..._ *Momyn ladingo..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Kada ki karantamin lbri matukar baki biya ba,In kika ka karanta batare da sani na ba na barki da Allah,in kina bukatar yin karatu cikin Salama ki nemi ta wannan Nombar wayar 09069067488_ *24*   """"Har Dare Zahra bataga Angonta ya leko ba,sai tafara damuwa,Saleema ce tace mata tayi hakuri zasu Shigo Shida da Sadiq kila idon mutane, ne yahansu shigowa tun dazu,Da farko tabar damuwa ammh data ga har pass 9 ai sai ta dau wayarta ta laluboshi sai taji ya sakata a call waiting.,lokacin yana waya da Malika ne,yana gani ya Shareta saboda yasan ko ya katse kiran, ba wata mgana bace mai muhimmanci ba,Shirme ne kawai da Shiririta. Zahra ko kamar ta Fashe saboda takaichi da bakinciki gefe guda,kuma wani Tarnakakin kishi ke dawainiya da ita gashi taki hakura da kira sai kira take yana sata a call waiting,ranta ko ya kara baci kamar ta Fashe ita kadai,kuma bai kirata ba,sai da yagama waya Da malika kana ya kirata,lokacin har kwalla sun Fara taruwa a idanuwanta. Tana Dauka Sai ta Fashemai da kuka,Shuru yayi yana Sauraranta cike da mamaki yace"Topha...Lafiyanki kuwa..? Tana Shesshekan kuka tace"Shine..Shine ina ta kiranka kaki dauka kana chan kana waya da wata ko..? Mele baki yayi kafin yace"Da wata kuma..? Ni bada wata nake mgana ba da yayarki ne,kuma bisa adalci duk wunin yau ban kirata ba,Kinga ko takirani ai na dauka na bata hakuri ko..? Wani bacin rai ya Shiga zahra sai ta danne kafin tace"Ok..Shine najika Shuru baka Shigo waje na ba..",Mamakin kalamanta yayi kafin yace"Haba don Allah Zahra mena ke ci na baka na zuba,akwai saboda rashin kunya sai na Wuce gaban Ummi da Abbi zuwa inda kike,tsayama su bakin dake dakin in na Shigo ina zasu..? Yafada cike da Dattako,Tura baki tayi kai tsaye tace"Toh su Fita mana.."Baki yakama kafin yace"Toh badani za'ayi haka ba,duk Abunda kikema Rawan kafa in inkinyi hakuri zaki sameshi zuwa gobe,sai kin barmin Abun Fada ba.." Ko ajikinta sai ma kara narkemai datayi tana Fadin"Toh Tunda kasan Abunda nakema rawan kafa mai zai hana ka min kwatantancen dakin sai nazo kabani ka Huta da Rawan kafan..",Tafada tana wani shafa Bakinta,Zaro ido yayi bai mata mgana ba kawai ya yanke kiran gabadaya yana kiran Sunan Allah,har Sadiq dake gefenshi yana waya da Saleema ya dago yana kallonsa,bai mai mgana ba,ganin ya dauki wayarsa ya Shige Tiolet,shiko wayar ya dauka saboda kada zahra takara kira,sai ya sanya Nombarta cikin blacklist ya dauro alwala ya Fito.. Jin ya kashe wayarsa,bai sa tagane tabargazan datayi ba,saima kara kokarin kiranshi datake,ammh ta gaza samunshi,tayi tayi taki Shiga kwata kwata,cikin damuwa ta Fito Falo ta Samu Saleema kan kujera tana waya ta daga mata duka tana Fadin"Ke kanwar Miji tashi ki rakani dakin yayanki yanzu.."Ba Saleema kadai hatta Nadira dake gefe tana charting sai da ta dago tana kallon Zahra cikin wani yanayi mai kama da kinyi hauka.. Saleema tayi Saurin yanke kiran tana kallon Zahra tace"Dakin yaya Saleem,lafiya kuwa..? Yamutsa Fuska tayi kafin tace"Kawai ina son ganinshi ne,ko laifi ne don nace kirakani dakinsa,ai naga dai an daura aure yazama mijina.."Tafada tana kallon Nadira,wacce ke kallonta cike da takaichi. Saleema tayi dariya tana kallon Zahra kafin tace"A"a ko daya,sai dai ni bazan iya wucewa dake zuwa dakin yaya Saleem ba,Su Ummi fa na falo,kuma bama haka ba wlh Yaya Saleem zai iya marina in na rakaki gwara kiyi hakuri ki kirashi ta waya.."Tafada tana sakin hamma,Jagale Zahra tayi kafin tace"Ina ta kiransa ban samesa ba...Tafada kamar zatayi kuka. Batama bama Saleema damar mgana ba,ta mike tana Fadin"Tunda bazaki rakani ba,ni bari naje da kaina,nasan bazan bata ba.."Tafada ta na kama hanyar Fita daga dakin,Nadira ta mike data ga rashin hankalin na Zahra ba karami bane,itako Saleema Abun ne ya bata mamaki,domin bata zata Zahran takai haka Wauta ba,Nadira ta sha gabanta tana Fadin"Wlh in kika Fita daga dakin nan,sai na kira Momi na sanar da ita,haba kidinga Abu kamar Wata mara Tunani da ilimi,in kin fasa Fita kin zama shegiya..."Tafada cike da masifa.,tana gama Fadin haka ta juya ta koma ta zauna tana sakin huci, Jin Abunda Nadira tace ne,yasa Zahra takasa Fita,sai ta joyu afusace tajuya koma ciki tana kunkuni,Sauran iyayenta kuwa kanzil ba wanda tace musu,sun so ne sai ta Fita wlh gari na wayewa su tatarra su koma Kano suce amarya ta Hutar dasu takai kanta daki,Saleema tabi zahra da kallo tana wani Tunani aranta na indai zahra ahaka take Tunanin Sace zuciyar Saleem,to da sake domin Yaya Saleem ba irin sauran sakarkarun mazan data sani bane,Mutum ne mai aji da takama,da Wuya su Shirya matukar bata gyara takunta ba,ganin haka yasa ta mike tabi bayanta,koda taje ta isketa ta kumbura kamar ta Fashe,saboda Fushi ita ta zauna tana ta bata hakuri tana kara nuna mata sai fa ta rage wani abu saboda tsaro,ammh suk zahra bataji tana ganin Abunda takeyi Shine Daidai.   ****************** Washegari Tun bayan Angabatar musu da Abun kari suka karya sukayi wanka kowa ya Shirya saboda su isa da Wuri don bazasu kwana a zamfara ba dagachan zasu juya kano ne,Itako zahra an cakare cikin wata Shadda Ash colour dinkin Riga da Sikat,kayan Sun fita da ita ba laifi,Ummi ce ta Shigo gaida amarya da baki,Allah ya kyauta lokacin tana Sanye da mayafi da anyi Abun kunya,ammh fa ita kanta Ummi tayi mamaki ganin amarya tana gaisheta zaune kan kujera ta mike kafa idonta kyar akanta babu alamun kunyar nan ta Surukai,Abun ya daure mata kai sai dai batayi mgana ba ta Share,ammh aranta tana Fadin"Wannan wata amaryace Saleem ya kwaso kuma..? Magana tayi akan Zata tafi da zahra chan wajen Abbi zai hadasu ita da Saleem yayi musu Nasiha ko gama Rufe baki Ummi batayi ba Zahra ta mike zumbur tana gyara mayafi tace"Yauwa Ummi muje.."Tafada tana yin gaba,ba Ummi kadai ba duk mutanen dakin sai da sukaji kunya,Tun ballatana Nadira taji kamar ta dora hannu aka ta yanka ihu,Saleema ko Wani iri taji don bataso ace wacce take goyon baya tana irin wannan Ba,duk zata bata musu Shirinsu Malikar ma ta Fita samun Fada wajensu Ummi. Ummi ko Yaken Dole tayi tabi bayan Zahra tana kallonta cike da mamakinta,gefe daya kuma tana Tur da wayewa irinta yan matan zamani,don yanzu sai ace wannan ba komai bane wayewar zamani ce,ganin Sun Fita kuma batasan hanyar ba,shiyasa tabama Ummi dama ta Shiga gaba suka hau sama har Falon Abbi inda yake zaune bisa kujera Saleem wanda ke sanye da Farar Shadda dinki Muhammed,Aikin jikinta baki ne hakama hulan kanshi baka ce,yana zaune akasa kusa da kafafuwan Abbi kansa akasa alamun biyayyah da ladabi.      Suna Shiga Falon Tunda zahra ta hangi Masoyinta ta fara washe baki,sai kawai tatafi kusa dashi zata zauna,kanshi na kasa ya dago yana hararanta cike da takaichi,ganin haka yasa Abbi fadin"Kyaleshi diyata dawo nan.."Ya fada yana nuna mata dayan gefen,Ranta baiso ba takoma nan ta zauna tana kallon Saleem cikin so da kauna kamar ta jawoshi ta Rumgume haka takeji,balle yadda yayi mata kyau yau sosai..    Ummi dake tsaye gefe ta rike haba tana Fadin Cikin ranta"Allah mai zamani..."Zahra saboda shagala da kallon Saleem bata iya gaida Abbi ba,sai Shine yake gaisheta yana tambayanta ya kwanan bakunta,sai lokacin ta danji kunya ta sunkuyar dakai tana ansawa,ammh kuma ta gefen ido tana kallon Saleem,shiko kunyar Duniyace ta isheshi gaban Ummi da Abbi,kan Abunda zahra tayi gabadaya sai yaji auren ma ya Fitarmai aka yarinya kamar mai tabuwar junnu.   Nasiha sosai Abbi yayi musu,Yayima Saleem nasihan adalci a tsakanin matansa,Tunda Nauyi ya hau kanshi sai ya dage,banda nuna bambamci kowani wariya ga daya daga cikinsu duka matanshi ne,daga karshe  yajamasa kunnen sai ya jajirce dole yazama na Namiji don zama da mata biyu babu sauki,don ko Shi da yake ubanshi daya gareshi,Yayima zahra Fadan tabi mijinta tamai biyayyah Shine Ribanta da Tsiranta aduniyama Har zuwa ranar Gobe kiyama. Kuma yayi mata nasihan ta zauna da abokiyar zamanta Lafiya ta kuma bata girmanta,wanda ko Ummi ma da Abbi yabata damar mgana Abunda tayi ta jadaddamata kenan,Sakale tayi kawai tana jinsu ammh azahirin batu hankalinta baya tare dasu yana chan tana Tunanin yarda zata ci uban Malika ne hankali kwance,Duk Nasihan da suke mata bata jiba,Domin tace duk suyi su gama miji dai natane ita take da ikon Sarrafashi yadda taga dama basai wasu sun tsara mata ba.   Bayan su Abbi su sallamesu Saleem ya Dukar dakai yana godiya kafin su tashi su Fita,suna Fita zahra tayi zaraf ta riko hannunshi tana sakin mai mirmishi cike da salon makirci,Fizge hannunshi yayi yana kallonta kai tsaye yace"Zahra..Wai mike kanki ne? nan fa gidan iyayena,haba kidinga Abu kamar wata kilakin karuwa,dubi abunda kikayi dazu agaban su Abbi,yanzu Fisabillahi haka h amare masu kunya keyi tsakani fa ga Allah.."Ya fada cikin bacinrai. Tura baki tayi kafin tace"To menayi kuma? ai ba Rashin kunya bane,suma su ummi murna zasuyi Ina son dansu sosai.."Kuramata ido yayi kafin yajamata wani dogon tsaki ya Kama hanya yana saukowa daga Steps da hanzari ta biyoshi har suka sauko hanyar dakinshi ya nufa,tako biyoshi jin tana biye dashi ne yasa ya waigo yana kallonta ganin ya tsaya ne,yasa itama ta tsaya tana kallonshi,Fuskarshi ba fara"a yace"Lafiya ina zaki naga kina bina ne...? Rausayar dakai tayi kafin tace"Ina kuwa..? inda zaka mana.."Turbene Fuska yayi kafin ya nuna mata hannu yana Fadin"Kinga malama Wuce ki koma daki yanzu zamu tafi gidanmu sai kije chan kiyi ta rashin kunyarki,ammh wlh bazan bari ki barmin Abun Fada gaban dangi da iyaye na ba,karki sake ki Biyoni wlh.."Yafada yana Jadadda bayaninsa,Kafin ya juya ya Shige dakinsa ya banko kofa yana Ma kanshi jajen ya auro ma kansa jaraba da kudinsa.   Ganin ya Shige ya barta yasa taja kafafunta takoma cikin dakin tana wani bata rai,ba wanda ya kalleta sai Saleema,wacce ke mata kirari cike da Iya Shege,nan da nan ta Shiga washe baki kamar wata sakarya,Yadda suka zo haka suka dauki hanyar Zamfara,ammh wannan karon babu  Saleema,wacce har ta Shiga mota Saleem yamata jan ido yace ta Fito,Tana tura baki ta Fita yayi mata kaca kaca,lokacin da Tajema Ummi tana kukan yahanata zuwa gidanshi,Shiko yace sai dai ta mutu Tunda ba uwar wani Zatamai ba intaje,dole ta hakura tanaji tana gani suka Fice daga haraban gidansu. Sadiq shi ya sake daukan amarya sai motar gidansu Abbi da direba guda daya,Sai motar haya guda daya,wacce Saleem yayi tashanta,daganan Zamfara Kano zata Wuce dasu,Sun riga Saleem yin gaba,don shi kadai yataho amorarshi ammh bayan ya kira Malika ya sanar da ita suna bisa hanya,Ummi ko bata barsu haka ba,ta basu Turamen zani guda goma,da Turaren Wuta,dana daki,sai kudi ta ba masu kawo amayar aka rabu cikin girma da arziki.   ****************** Lokacin da Saleem ya kira Malika Tuni har an gama mata kunshinta ja da baki da kitsonta 2Steps😂,wanda yayi mata kyau over sai wanda yagani kunsan Farin fata yana karban Jan abu da baki atare,sai kitsonta wanda ya kasance yiri yiri ne,dama akwai gashi sai ta fito ras da ita,Abu daya yayimata cika katon Tulalen cikinta,wanda tayi wanka ta Shirya cikin leshinta riga da zani ta kashe daure bakace Malika malik din nan bace mai sanya kananun kaya masu Fitar da tsiraici. Tun jiya su goggo hadiza suka iso ita Zulai tare da suka taru dasu Maman Abba suka sha bikinsu ajiya,suna kuma kokarin Debemata kewa sosai,wanda yayi nasaran ragemata damuwa,da kuma kishi,duk da taji abun,mussaman da lokacin daura aure ya kusanto har yazo ya Wuce,taji Abun aranta,ammh basu barta Tashiga halin damuwa ba,Hatta Hajiya binta dake gida tana takaba sai da ta kira Malika tana kara tausanta,Mirmushi kawai malika take aranta tana Fadin"To in batayi hakuri ba, ina zata da wannan cikin,ko tabar gidan Saleem bamai kwasanta ya zauna da ita don Allah,saboda haka hakuri yazama dole gareta.   Yana sanar da ita tasowarsu ta sanar dasu Joda,suka fara shiryen Shiryen taransu,duk da dama chan ashirye suke,gidan suka kara gyarashi sosai kafin su shiga kichen su dukufa wajen shiryama yan kawo amarya delious mai dadi cikin mutumci da kima. Basu iso ba sai wajen 2 na rana suka iso,wanda Malika najin Sautin hon dinsu da kuma karar bude get,gabanta ya amsa ta tashi da Sauri Ta shige daki tana kokarin danne Abunda ya tasomata,Su joda da Maman Abba ne da Su zulai suka Fita suka tarbesu,Zahra dake cikin mayafi hankalinta na kan karema gidan da kallo,Haka take bin ko'ina da kallo har suka Shiga falon gidan suka zazzauna ana gaisawa ana tambayan gajiyan hanya,Joda ce kan gaba ta nuna musu dakin Zahra wanda ke kusa dana Malikan suka tashi suka Shiga da Zahra ciki,wacce dama ta kagu akaita dakinta taga wani iri ne. Dakinta yana da girma,Shimfide da wani cafet mai taushi,wanda ya mamaye dakin gabadaya sai makeken rolay bed dinta da kuma Wardrope mai girma da Fadi,sai dressing mirror,sai kofar Tiolet,zahra a wulakance take bin dakin da kallo,Bawai dakin bai mata bane a"a so take taga na ita malikan ya yake? don ita zatonta Saleem ya raina mata wayau Ne Shiyasata ya sanya  awannan dakin wanda da kadan yafi na gidansu inda take kwana. Joda da Maman Abba da Zulai su suka dinga kwaso musu kololin abinci zuwa cikin dakin Zahra inda suka ga Abun mamaki amarya ta zaune kan tsakiyar gado ta cire dankwali shigen gashinta mai kama da Hammatan dan iska awaje,duk ya mike Kallo kowa daya daya take tana wani girgiza kafa,Maman Abba da joda suka kalli juna suna mamakin wannan al'amarin daga zuwa har za"a nuna hali,sai da suka Fita zahra ta kalli Nadira take cemata"Wai yan biki kenan,? hala bata da wasu dangi ne ita Malikar,koda yake sai dai in taron arna..," Tafada tana yar karamar dariya,Tsaki Nadira taja tana Fadin"kedai kike kidanki da rawanki,in banda Shiga Abunda bai shafi mutum ba,ina Ruwanki da danginta,kedai tafi wajen Shigen rawan kanki da Shisshiginki miji ya ram miiki,kinga ko kya ga karshen Rawan kai.."Goggo Shatu tace"Kwarai da ma gaske,ai tama baras,Nadira tunda ta yada hali gaban Uwar miji,mai ya rage kuma,ai babu Shi Nadira,Allah dai kawai ya sauwake..." Zahra ta tura baki ta kauda kai tana dauko wayarta tacigaba da Laluban Nombar, Saleem ammh har yanzu bata Shiga kuma,sadiq yace batare suka taho ba shi yana baya gajiya tayi da kira ta hakura takoma gefe tana kallonsu Nadira na cin abinci,Farar Shinkafa,da miyan nama,sai Fride rice,sai kunun aya mai sanyi,da ferfesun Naman kaji,kallonsu take don ita babu abinci agabanta so take ma suyi su tafi abarta daga ita sai angonta.    Sadiq kuwa Joda tayi ta dawainiya dashi,bayan tabashi na Direban da zai maida Su Nadira ya kaimai,ya dawo yazauna falo yana cin abinci yana ma Joda hira har yana tambayanta Shi bai santa ba? tace mai ita kanwar Malika ce gidansu daya,Sai alokacin Malika ta Fito tana taku dakyar suka gaisa Da Sadiq yana kara kallonta kamar ba ita, ba kamar wata zara acikin wata,shi baima san cikinta ya tsufa ba haka don Saleem baya yarda yayi mganan Malika dashi,koshi ya jawo hirar Kauceta yake,ya basar.   Suna cikin gaisawa da Sadiq din sai ga Saleem ya Shigo gidan yana waya,yana sagale da yar jakan kayansa,Sai da ya katse wayar ya kariso garesu yana bama Sadiq hannu suka tafa yana Fadin"Kai mutumina kayi Wuta ahanya fa.."Yar dariya Saleem yayi kafin yace"Ah to mezan jira,ai ban saka lerna ba,balle na dinga na lallaba Titi.."Yafada yana kallon Malika dake tsaye tana gyara zaman mayafin kanta,Kwabemata Fuska yayi kafin yace"Ba sannu da zuwa Yar Amanata.."Batayi mgana ba,illah karisawa datayi gareshi tana saka hannu ta karbi jakan hannunsa tana Fadin"Yanzu fa ka shigo.."Sannu da zuwa.."Kin sakin mata jakan yayi saima Rumgumota dayayi ta gefe yana Shafa fuskarta yace"Bar jakanan kawai kinyi Nauyi dayawa kada na zama mara tsausayi.." Ya fada yana shafa cikinta lokaci daya yake Fadin"Kai cikin nan yayi kasa sosai,koda yau zai Fito Duniya..? Sadiq ne yace"hhh karma kayi Fatan haka don zaka tashi daga angon amarya ka koma angon karni,wlh baka ba kwanan dakin Amarya sai dai kwanan Asibiti.."Dariya joda ta saka,shiko murmusaa kawai yayi Malika bata hakura ba jakar ta sake karba ya sakarmata yana kallonta Mirmishi tayimai tana Fadin"Kada kahanani samun lada awajen Allah..."Hannunsa ya daga yana Fadin"Wane ni? ai ban isa ba,Allah yabamu ladan dukkanmu.." Batayi mgana ba. ta Wuce zuwa dakinshi,shi kuma ya tsaya suna gaisawa  da joda da maman Abba data Fito yanzu sai Zulai wanda dama Malika ta sanar dashi zuwansu,har dakin Malika ya shiga suka gaisa da Goggo hadiza yana mata godiya,Yana Fitowa dakinsa na yawuce yabar Sadiq zaune yana mai tsiya,koda ya Shiga dakinsa nasa,ya tarar da har Malika ta hadamai Ruwan wanka,Mamaki ta bashi yadda yaga cikinta ya tsufa dayayi mata mgana sai tace zai hanata neman lada,sai ya kyaleta bai samu lokacin yaba lalliinta da kitson ta ba,sai da yayi wanka yayi sallah yaci abinci kana,haka yadinga Sumbatar hannu yana Shafa kanta,nan take ya bata 5k yace tabama wacce tamata lalli da kitso,domin zahirin batu yagani kuma ya yaba.    Sai wajen biyar na yammah yan kano sukayi Shirin tafiya,bayan sun gama jerama Zahra akwatunta sun mata yan nasihu duk da sun san baji zatayi ba,Nadira tayi kwaba tayi kwaban kamar bakinta zai Cire,ammh Zahra sai ta nuna taji,ammh kuma nan ko bata jin zata dauki mganarta,da zasu tafi sukace Zahra ta Fito su mika amanarta ga Malika,ammh sai zahra tace Allah ya kyauta tabi kishiya,sai dai in Malikar ta matsu ta shigo dakinta ayi mganar,ganin haka yasa babu wanda yakara bi ta kanta,da zasu tafi har dakin malika suka shiga don su gaisa lokacin tana dakin Saleem,sai da joda ta Fita taje ta kwankwansa musu ta kirata tazo suka gaisa cikin mutumci,daga karshe sukace ga Zahra nan kanwata take gareta,don Allah tayi hakuri da ita,su zauna lafiya da juna,don su samar ma mijinsu zaman da kwanciyar Hankali,sunji dadin yadda Malika ta karbesu sai sukaji ta burgesu sosai,domin ba haka suka samu lbrinta ba,domin ance bata da dabi"a sam,sai suka ga sabanin Tunaninsa,dazasu tafi haka sukayi ta sakamata Albarka da fatan Allah ya sauwaketa lafiya. Sai da suka Fita haraban gidan kana Saleem ya Fito sukayi sallama ya basu kudi 3k sukuma Su joda suka Fito da Musu da kaji da meatpie da donout,din da sukayi musu wanda sukayi raping dinsu,suka basu suna ta godiya,Nadira dai mamakin ganin Malika take da ciki,don batajin ko Zahra tasan da cikin nan,don data sani da ta sanar da ita,Abun mamaki sai ga amarya acikin yan rakiya tana Rumgumesu tana daga musu hannu ammh Fuskarta babu alamun Rashin jin dadi ko Kuka ko damuwa,a'a fuskarta cike da Annuri. Suna tsaye motarsu tatashi suka Fice daga  haraban gidan Zahra na daga musu hannu,sai alokacin taga Malika wacce datake bayan Saleem,sai yanzu ta Fito ta gefenshi gabanta ne ya Fadi ganinta da turtsetsen ciki,wani karin Abun takaichin ma hannayensu sarke dana juna suna mgana kasa,kasa malika ke sakin mirmishi Daga ganin Wata mgana mai dadi yake gayamata. Duk da ahoto tataba ganin Malika bata zata afili tafi kyau ba,koda ita da datake amarya bazata Nuna ma malika kyau ba,duk da ko cikin jikinta wanda yake hanata kwalliya,Babu karya kyanta ya daki zahra sosai balle ma cikin dake jikinta wanda ko Saleem bata sanar da ita ba. Itako Malika Tana kallon Zahra ne cikin ilimi da wayewa,daga sama har kasa,tabe baki kawai tayi cikin ranta batace komai ba,Ganin yadda ta kura musu ido ne yasa Malika tayi kokarin Fizge hannunta tana nuna mai Zahra da baki,dagowa yayi yana kallon Zahra wacce ta harde hannu akirji tana kallonsu Fuskarta babu Fara'a ko kadan. Da Sauri Malika ta isa ga Zahra tana mata Fara'a tace"Sannu da zuwa amaryarmu..."Tafada tana bata hannu su gaisa,baya zahra tayi da hannunta tana ma malika wani kaskastancen kallo na Wucin gadi kafin ta mele baki tana Fadin",Yauwa sannu dai buh found of correction Hajiya malika amarya Saleem kabir kumo kidaina saka min jaye.." Tafada tana wani yamutsa Fuska kamar taga kashi,wani nauyi da kunya suka kama Malika ta sauke hannunta asanyaye tana mirmishin yake kafin ta kada kai kawai ta Wuce cikin tanajin yau fa kenan,? lalle akwai aiki ja agabanta game da amaryan mallam,Shiko Saleem waya ya tsaya yanayi wanda Sadiq ne ya kirashi yana sanar dashi har ya kusa isa garin Abuja motarshi ta samu mtsala,ammh zaiyi ma bakanikensa waya,shiko yanzu zai bi motar haya zuwa Abuja,so duk Abunda yafaru baida masaniya,yana kokarin yanke kiran ne yaga Malika ta wuce cikin gida,itakuma ta zahra ta matso inda yake tana mai wani kallo kamar ta lasheshi danye bai gasu ba Tana karisowa kusa dashi ya yanke wayar yana binta da kallo,riko gefen hannunshi takama Tana Fadin",Haba Honey Shikenan kuma tun jiya bankara ganinka ba..."Tafada tana saka kanta bisa kafadanshi,ganin megadi awajen karya dizgata yasa yadan riketa suna tafiya zuwa cikin gida yace"Ai yanzu ina tsammanin korafi ya kare ko? Tunda gaki gani,naga Yar Amanata taje kun gaisa,hop kin gaisheta da kyau Antynki kenan Malika Abdulmalik dankasuwa matata ta farko kuma uwar ya'yana..' mganar ta zafeta Shiyasa ta tabe baki batace komai,shima ganin haka sai yaja bakinshi yayi Shuru,suna shiga falon suka iske Joda da Maman Abba,sunsaka hijabai zasu Fita da alama zataje gidan Maman Abba gabadayansu ganin Zahra rike da angonta Abun yabasu matukar mamaki sudai a al'adan bahaushe amarya tana kunshe adaki tana fargaban zuwan angonta,wasu ma saboda kunya ko siyan bakin akayi basu iya budeshi suyi mgana,ammh yau agidan Saleem suke ganin wani sabon salo,ai Tusa da lasifika😂 Irin kallon da suke binsu dashi ne,yasa Saleem dan jin kunya yana kokarin raba rikon da Zahra tamai ammh taki sakinshi saima kara kwantar da kanta take bisa kafadanta,Girgiza kai kawai yayi yana basarwa nan sukayi sallama da Maman Abba,wai ashe Zulai da joda ta dauke zasuje gidanta su tayata kwana Abba da babanshi suna zaria wajen maman mijinta,Goggo Hadiza kadai aka bari,wacce duk kunya saleem ya takuramata tana cikin dakin Malika bata ko Fitowa falo,takuma gayama malika gobe da Safe zasu koma malumfashi insha Allah. Har su joda suka Fice bata sakeshi ba bai sake mata mgana ba,illah hanyar dakinta daya nufa,sai da yabari sun Shiga kana ya Saketa yana kallonta kafin yace'"Wai miye haka...? Sakarni alwala zanje nayi na samu jam'i kema ki gagggauta yin naki sallar.."Tura baki tayi tace"Toh ina zaka? baga tiolet anan ba,ka shiga muyi alwalan tare.."Tafada tana kokarin kwantomai bisa kirji,ganin haka yasa yayi Saurin Fadawa tiolet ta biyo bayanshi sukayi alwala yana Fitowa yayi hanyar Fita tayi zaraf zata biyoshi ya waigo cikin haushi yana Fadin"Ina kuma zaki bini..Ehe..? Diddira kafa tahauyi kafin tace"Inda zaka mana,don naga baka da niyyar sauken alqawarin dakama iyayena wajen kula dani da rike amanata...",Tafada harda matso kwallar Karya,kansa ya dafe kafin ya karisa gareta ya riko hannunta yana Fadin"Injiwa... ? wayaga miki bazan kula dake,kinga ana kiran sallar mangariba,sauri nake naje na samu sallar cikin jam'i ko baki son ace mijinki yana kokarin yin sallar cikin jam'i.."Kallonsa tayi kafin tace"Ina so mana.."Da hanzari yace"Toh kibarni naje nayi na dawo,saurin mekike,yau ba tare zamu kwana ba..",Da hanzari ta gyadamai tana Mai wani kallo,Sakin hannunta yayi yana gyara hulan dake kanshi yake Fadin"To kingani,oya Kema kiyi sallah asakemin wata sabuwar kwalliyan wannan ban Amince inci amarci da ita ba.,Sai na dawo.."Ya fada yana karisa Ficewa daga dakin,Sufa tayi ta haye kan gado tana Rumgume Filo cike da murna,cikin rawan jiki tatashi tayi sallar ta Tube kaya ta Fada tiolet tayo wanka akazo aka shafama lotion kafin abi kowani lungu da sako na jikinta da Turare,Wai saboda rashin hankalin zahra wai Tunda Saleem yace ta sake kwalliya to kwalliyan kayan barci yake Nufi batayi sanya ba ta bude akwatunta na inners ta zabo wata arniyar riga wacce tsawonta bazai gaza cinyarta ba,gata da budadden gaba,gata kuma raga raga,pant kawai ta sanya babu bara,sai ko gabadaya halittan kirjinta suka bayyana waje,tana kallon kanta amadubi tana jujjuyawa take fadin"Haba dole ya raina kansa in yaga wannan kayan,yasan nawa ba irin nata bane..." ***************** Shiko Saleem bai dawo gida ba,sai da yayi sallar issha'i kana ya dawo,kuma koda ya dawo bai Shiga dakin kowa ba sai yawuce dakinsa yayi wanka ya sanya jallabiyansa Mai Ruwan toka kafin ya dauki wayarsa ya kira Malika yace tazo dakinsa ta sameshi yanzu,bayan ita sai ya kira Zahra yace itama tazo dakinshi ta sameshi yanzu,Jin kiran dayake mata sai bata kawo cewa harda Malika ya kira ba,ita atunaninta kila chan ne zasu first nigt dinsu😂ai bata tsaya sauyawa kaya ba sai ta kara gyara fuskarta gyalen kawai ta yafama kanta,bata kuma Fito ba,sai da ta kada wani garin mgani tasha da madara kana tafito tana rarraba ido,ganin dakin daya ke hari dazu sai ta sa aranta nan ne dakin saleem din. Da confident dinta ta Shiga,Cikin Siririyar Sallamarta,Turus tayi ganin Malika zaune akasa ta mike kafafunta,Shikuma Saleem yana rawan jikin jeramata Filulluka,bayan yagama yakoma mtsamata kafa,yana mata mgana kasa kasa,cikin ran zahra tace durun uwa Salatin Arna😂😹ita za"a torzata,tsaye kawai tayi hannunta bisa kugunta tana jifansu Da wani mugun kallo,Malika ce ta ankare da ita sai ta tabo Saleem ta nunamai Zahra,ganinta ahaka kafafu duk awaje yasa ya zaro ido😳😳Lokaci daya yana Fadin",Zahra lafiyanki kalau kuwa..? Kinga yadda kika Fito marabanki da tsirara kadan ne.." ,_*Hhhhhh...Kuna bani dariya masu cewa kila Zahra ba budurwa bane,? waya sanar daku haka,? ai bance Zahra na bin maza ba,Nadai ce Tana da rawan kai da Iyayi da Feleki,Sai kuma rashin wayau dake damunta,in kun lura akwai irinsu Zahra sangartattu marasa wayau da badon ta samu jajircewan Uwa da uba ba,ga kuma Nadira dake kwabamata ba,da yanzu tafi haka Wauta itafa duk Abunda take yi gani take Shine zai sa Saleem yasota fiye da malika ya haukace mata,ita bata Tunanin tana kashe kanta ne,irin sune inda a kauye aka Haifesu da yanzu sun Fara Shiga Daji*_😂😘 *Momyn ladingo..*😘 *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *25*   ""Kwabe Fuska tayi tana wani kif-kifta ido tace"Kamar ya marabana da tsirara kadan ne? Yo inace bakai ka kirani ba,kuma laifi ne don mace tazo Turakar mijinta tana kama da Tsirara kamar yadda kace..",Tafada tana jifan Malika da wani matsiyan kallo na zakiji ubanki ne,ke kikafi bani haushi.   Wani miyau Saleem ya hadiye yana Fadin"a'a ni bance ba,kariso dama na kiraki ne, don kizo na gabatar dake ga malika na kuma taraku nayi muki nasihan zama lafiya da juna kamar yadda al'ada ya tanadar.."Tabe baki tayi kafin ta kariso tana wani jijjigen jiki kamar wata mara hankali,gefen gado ta zauna tana kada kafa,Fuskar na gefe tace"Ina jinka yi da jiki don inajin barci gaskiya.." Daga Saleem din Har Malikan da kallon tababbiya suka bita,tun ballatana ma Malika wacce take ganin alamomin zahra kamar wata bakauyiya wacce batayi ilimi ba,Saleem ne yaga iskancin nata yayi yawa shiyasa ya hade rai kafin ya fara gabatar musu da juna,ya gangaro zuwa Nasihan su zauna lafiya,bangaren zahra ya juyo yana mata mgna da kakkausan murya inda ya Sanar da ita bai aurota don bayason matarsa ba😂🤔kuma bai auro ta don ya gaji da ita ba,ya auro tane don koyi da Annabin rahama sallalahu alaihi wsallam,kuma yayi mata mgana da zafin rai na kada ya kamata da Raina malika ko rashin kunya da rashin da gareta,ya gayamata koda ba domin tana uwargida ba,Malika ba tsarartabace ko banza agirme ta girmeta,so ta girmama ta kuma ta bita sau da kafa,daga karshe ya sanar da Malika sai tayi hakuri da Zahra kanwace gareta,Wani abun sai ta dinga Nusar da ita. Malika bata bw Saleem kunya ba,tayi mgana cikin Hikima da natsuwa,itako Zahra saboda bakincikin kalaman Saleem na wai tabi Malika sau da kafa,yasa ranta taji yabaci da"aka nemi tayi mgana tana cin mgani tace"Naji duka maganganunku,sai dai Abu dayane bangane ba,Matarka Malika ce ta biya Sadaki ta auroni,ko kuwa kai kaine ka auroni da kudinka..? Tafada tana kallonsu dukkansu,Saleem yaji kawai ransa yabaci cike da kosawa yace"Wannan wata irin Tambayace? look zahra kingani nan dagani har matata bamasu son Rigima bane,indai ke rigima shine sana'arki to wlh bazamu Shirya ba.."Yafada yana Nurfafashin bacin rai. Adage zahra ta kalleshi kafin tace"Au Allah,wato bakusan Rigima gani ni kuma Fitananniya,toh ni ba Fitinanniya bace gani nayi kana wani sanar dani nabi matarka Sau da kafa,alhali ko agida da za"a min nasihan zama da kai,wa mijina kadai ace nayi biyayyah baga wata katuwar gardiya ba.."Tafada tana wani mele baki,Ran Saleem yabaci saboda kalaman Zahra,yana kokarin mikewa ne Malika ta rikemai hannu tana Fadin"Plz don't say Antytin...ba girman ka bane mallam.." Tafada cikin sanyin murya,tana kuma kallonshi cike da sanyinta,Ganin yayi Shuru ne yasa takara damke hannunshi tana Fadin"Tadani na tashi,kasan ita amaryar so ce,so yar lallashi ne,don Allah Kayi hakuri kada ka biyemata yarinta ne ke damunta.."Tafada tana cije baki,zahra dake zaune ta zaburo tana Fadin"Eh naji yarinta ke damuna ai gwanda ni dana tashi sai na iyama kiruciyata banje na auri wanda yayi kusa da Sa'a na ba.."Tafada tana girgiza jiki lokaci daya tana sanya hannunta bisa kugunta,ko kallonta Malika batayi ba,Saleem ya taimakamata tatashi tana cije baki yana mata sannu,zaman myafin kanta ta gyara tana Fadin"Sai da safe Mallam,plz Amarya Kiyi hakuri fa,asha amarci lafiya.."Tafada hankalinta kwance kafin ta zame hannunta ana Saleem ta Fice daga dakin tana takawa dakyar saboda Nauyin datayi. Tana Fita Saleem ya juyo ga Zahra yana Fadin"Tahaka zamu fara dake..? lalle ko ki chanza taku in ba haka ba wlh zamu samu mtsala cikin kankanin lokaci,don ni kingani nan na tsani mutum mara kunya da kuma girmama na gabanshi,uwa uba kuma rashin biyayya,ina mijinki wanda aka kawomin ke yau,ammh ina mgana kina maidamin da amsa kamar wani tsaranki ko? karki shiga hankali Allah zan saita miki kanki dinnan dake rawa bai zama daidai ba,mark my words.."Yafada kafin ya juya ya Shimfida darduma yana fadin"Ki Wuce kije ki sanyo zani ki kuma dauro alwala kizo zamuyi salla ne.." Tsaye tayi tana kallonshi kamar zatayi mgana sai kuma ta fasa,Ganin irin kallon dayake mata,tana Tura baki ta Fice zuwa dakinta ta dauko zani ta daura bisa Rigar barcinta tadawo dakin,a tiolet dinshi ta Shiga alwala aranta tana fadin,ai bazan bari acuceni ba,daga yanzu har zuwa na cinye kwana bakwai dina adakin mijina zan dinga komai,ai itama ta shana,sai ta barni naci lokacina😂Koda ta Fito ta iske yana jiranta nan yajasu sallar Nafila Raka'a Hudu sukayi kafin ya sallame ya yi musu addu'a,Abun ya dauremai kai ganin duk tambayan dayayi mata game da addinta ta amsashi daidai babu kuskure,ammh ji Abunda takeyi sai kace batataba zuwa Mkrantar koyon Addini ba.   Nan kan Dardumar ta barshi ta haye gado,wai barci takeji,yana kallonta ammh takasa barci sai juye juye takeyi tana kallonshi,yana lura da ita yayi mirmishi cikin ranshi yana Fadin"hmm zaki samu Abunda kike nema,don wannan in ban bata Abunda take so ba,zuwa gobe zata iya kiran gida tace ban kusance taba,Tunda ya lura bata da cikakken Hankali. Sai da yakoma Tiolet yayi bursh,kafin ya koma dakin,jallabiyan nashi ya cire yarage dagashi sai dogon bakin wandonshi ko vest bashi ajikinsa,ganin Faffadan kirjinsa awaje yasa take kara kallonshi kamar tajita kwance akan kirjin tana Shafawa,yana lura da ita ammh sai yayi kamar bai ganta ba,ya hayo gadon Agefe ya kwanta bayan ya saka hannu ya kashe hasken wutar dakin ya kunna Dumlight Blanket din dake gefe yaja ya lullube rabin kafafunsa,dashi kafin ya tara duka hannunwanshi yana Addu"an kwanciya barci,Zahra na jinsa tayi lambo tana hadiyan miyau kamar wata mayyah,Tana ganinsa yashafama duka jikinsa kafin ya juya mata baya,ganin haka yasa wani kulikulin Takaichi ya ciyo Zahra,,yanzu kamar ita Ace Namiiji na juyamata baya,duk uban Tanadin datayi saboda shi,wlh bazata yadda ba,cikin sanyin murya ta kira sunanshi.   "Honey...Kayi barci ne..? Yana jinta yayimata banza,ganin haka yasa ta gangara zuwa gareshi ta Rumgumeshi ta baya tana sakin ajiyar Zuciya,bisa wuyansa ta zura hannunta tana Shafawa zuwa keyarsa tana Fadin"Honey Shine kayi kwanciyarka ka kyaleni ko..? Tafada cike da Shagwaba da sangarta,Ganin yaki mgana ne yasa,ta zura hannunta wajen kirjinsa tana Shafa gashin kirjinsa cike da salo,lokaci daya tana shafo Nipple dinsa,yaso ya Doje ammh jin abubuwan datakemai ne yasa dole ya Juyo yana rikota dakyau cikin wata irin murya yake Fadin"Kibar rawan kafa,Abun ba dadi ne dashi ba adaren Farko.."Yafada yana Shafa bayanta zuwa kugun hips dinta,cike da mugunta yake Sumbutar Wuyanta,yana kuma kara kaina da hannayensa cikin sassan jikinta,Tun Zahra na iya madamai da martanin salon wasan nashi haryazo ya kure Tunaninta musamman ma wajen dayake Tsotsan Nipple dinta,Bankare bankare tafaramai tana wani Numfashi sama sama,yafi minti talati yana Yana wasa da ita kafin ya fara neman hanyarshi,Zahra duk azatonta Abun mai dadi ne, sai da taji Wani abu na zungurinta kamar icce,kuma daya zungureta sai taji wani radadi,kamar an zubamata barkonu awajen,Jin Abun yana kara yawa ne yasa tafara mutsun mutsun kwace kanta,tana hade kafafunta,shiko Saleem da gayyah ya taleta dakyau😂ya kuma Rufe mata baki ya danna kai,Ai zahra ji tayi kamar ana sakamata reza ne ana caccaka wajen,gashi tana so tayi ihun ammh yatoshe mata baki,Tun tana iya motsu motsu har tazo jikinta yayi laushi Haka yake gurzarta kamar Allah ya aikoshi,dayayi Realising sai ya kara koma mata kamar wani maye,kuma ba komai bane ya jawomata haka sai shayen shayen mganuguar matar datayi,wanda dama akida in kikasha sukayi miki yawa toh ranar Mijinki zai Wuce mintinar dayake wajen saduwa dake yayi ta Abu daya ba gajiya,ke kuma nadama zata Shigeki sanda yayi raga raga dake,wajen neman ido ki rasa gira,koda yake basu nadamar haka sun gwammace suyita Shiga Ruwan zafi suna jinyar kansu,sudai burinsu ya cika Tunda miji yayita nanike musu ba gajiyawa. Abagaren zahra kan tayi Nadama yafi cikin kwando Dubu don Allah kadai yasan yawan Allah ya isan data dinga lurama Saleem acikin zuciyarta,Jikinsa ko yasha yakushi da kunbunanata,kuka tayi shi har saida tagaji don kanta ta hakura,majina da hawaye suka dame waje daya,shiko Saleem bayama jinta caccakarta kawai yake jiyake kamar karfinsa na kara hauhauwa ne,kamar na doki,ga kuma mganin matan datayi amfani dashi wanda ya Yi sanadiyar Kara Fitar dashi daga hayyacinsa har sai da yayima zahra ci biyar Adare daya akuma lokaci daya,kafin ya koma gefe yana maida numfashi wahala,lokaci daya tambayan kansa anya Shine kuwa? domin yafi kowa sanin kanshi koda yake da karfin sha"awa bai da tsawaita kai Farmaki duk dadewarsa Minti talati koda malika ne,itama ta sani ammh kuma Abun mamaki Tunda ya hau kan zahra yaji yakasa control din kanshi d more zaiyi realesing d more,wata sha'awar ke kara zuwarma yayi mata Abunda ko Malika da zai yi Ramuwa akanta bai yi mata wannan cin haukan ba,Tundga nan ya fahimci akwai lauje cikin nadi,kuma yazama dole ya Tuhumi zahra kota gayamai gaskiya me yajawo haka?ko kuma wlh yaci ubanta la ada waje babu Ruwanshi. Yana jinta tana Shesshekan kuka ya barta ya Shige tiolet ya sakarma kanshi yayi wankan tsarki ya Fito,yana tsane kanshi da karamin towel dake hannunshi ,yake kallon Zahra wacce ke kuka tana yarfe hannu,muryanta ta Dishe take Fadin"Wayyo momi,wayyo Abbana..Wayyo my best kuzo ki ceceni ya kashe ni Allah ya is Mugu kawai Azzzalumi wlh bazan taba yafe maka ba.."Wani haushi ya kamashi ya daka mata tsawa yana Fadin"Ai ke zan ma Allah ya isa da kika zalunceni Zahra,me kika sha? kika saka nayi Abunda ba halitta bace,duk Abunda ya faru dake kekika ja,kuma wlh hakan yayimin daidai domin Abunda keke nemane kika samu,kuma kin san da sani wlh gobe sai kin Fadamin wani banke banken hauka kikayi ma kanki,gashinan kinzo kina neman kissheni ni kuma kisa na kasheki.."Yafada yana Nunata da yatsa,tana jin Abunda yace ta Wage baki ta saki kuka,Ransa yakara baci haushi ya cikashi baisan sadda ya isa gaban gadon ba,cikin Fushi ya Fizgota sai gata ta Diro da kan gadon kafafunta suka daki kasa,wani kuka ta saki jin kasanta yadda yake turirin azaba kamar anzuba barkonu,ganin haka yasa ya dagata cak,sai cikin tiolet ya direta fuskarshi babu Fara'a yace",Malama kibar kukan nan kiyi wankan tsarki ki Fito,kuma wlh kikayi yadda naji ko shesshekan kukan ki ne yadda kika batamin rai sai na Shigo har bayin nan nakara bayan nayi fatafata dake.."Yafada cikin kakkausan murya ganin yadda yake Huci ne yasa ta tsuge bakinta tana Sharan hawaye,tsaki yaja ya Fice da bayin. . Wutar dakin ya kunna,sai ya tarar da zanin gadon duk yabaci da jini hade da sperm tatarrashi yayi tana tsakar gasa jikinta taga yabude mota ya watso zanin gadon afusace yakoma,bayanshi tabi da kallo tana jin dadi aranta domin ko ba komai tanunamai Ruwa ba'asan kwando bane,ammh duk da yayi mata Abun cikin zalunci ne,ita da'akace mata Abun na da dadi,ammh ji Abunda Saleem yayi mata harda jini saboda mugunta,sai wata zuciya tace"Ke banza duk Dadinki ne yasa ya haukace miki yayi miki haka.."Jin haka yasa ta saki Dariyan jin dadi,duk ma sai taji azaban tatafi ta kara mikewa tana gasa kanta dkyau ranta Fes kare agado..😂 Shiko zanin gadon ya chanza,kafin ya koma ya kwanta Abun yaki barin ranshi,har Zahra ta Fito daga wanka tana Dafe dafen bango yana kallonta ta Dumligt din dakin aranshi yana Fadin",Baki dafa bango ba,zaki dai ki dafa gobe da safe..'Yafada yana cije baki yayi alqawarin Sai ya koyama Zahra hankali in ma mganin mata tasha daga yau yayi mata alqawarin ko sadaka aka bata bazata karba ba. Yana jinta tahayo gadon tana makyamayarta cike da Jin jiki,bai barta ba sai ji tayi,Yakara rikota Yana Shafa mata jiki,jikinta ne ya saki tafara matse kwallah,jin bai dauki wata hanya ba,yasa ta dan saki jiki,romancing dinta yashigayi da zafi zafi,tana jin dadin abu ya katseta ta hanyar Kara daidaita hanya,ai Sai Zahra ta haukace tana kokarin kwace kanta,ammh ina yayimata riko sosai ya danne bakinta danashi yashiga hakarta babu kama hannu yaro,Tun Zahra na iya motsi har tazo takasa kuka ma Rahama ne,haka takeji wani Siririn azaba na Fita daga kasanta ko kafin karfe 5 na asuba Saleem ya nemi Zahra yafi akirga,kuma lamarin nashi babu tsausayi sosai,har yaje sallar asuba ya dawo tana kwance tana kukan zuci,Kallonta yayi yana tsaye yake Fadin. "Nasan haryanzu baki gaji ba kona kara ne...? Jin haka yasa Zahra tafara jan jikinta baya tana hawaye,harde hannuwanshi akirji yana binta da wani kallon banza kafin yace"Au ai na zata haryanzu dakarfinki ganin irin shayen shayen dakikayi tayi ke ga amarya ko,zaki gayamin abunda kika sha ko sai na kara zuwa inda na Fito yanzu..."yafada yana dora kafanshi daya bisa gadon,Zahra tayi Shuru da bakinta taki mgana don ita haryanzu batayi Nadama ba. Ganin tayimai banza yasa yayi kamar zai haye gadon,da hanzari tadaga hannu tana Fadin"Don Allah kayi hakuri,Wayyo Allah na!Wlh in kakara zan iya mutuwa,don Allah kayi hakuri.."Mirmishi yayi kafin yace"Toh oya gayamin me kika sha ne haka,domin Abunda na aikata ba haka Karfin Desireta take ba..? Tana Sharbe hawaye tace"Magungunar mata nayi ta sha,tun ana saura wata daya bikinmu.."Tafada tana mtse kwallah,baiyi mamaki ba,dama hasashen shi ya bayyana Kada kai yayi yana Fadin"Gud,wato keda bakima Shigo cikin gidan auren ba,har kina tunanin yadda zaki sha mganugunar mata ki rikitani ko?ai kin Rikitani ni kuma nayi alqawarin nima sai na rikita ki,yadda zan Fitar da ra'ayin Shaye Shayen magungunar mata daga Zuciyarki,comon jere kitashi kije kiyi wanka kizo kiyi sallah..."Yafada yana kwanciya agefenta. Zahra na kuka haka ta rarrafawa zuwa Tiolet tanayi tana cije baki,haka ta gasa jikinta tana kuka,ammh saboda taurin rai irin na Zahra babu Nadama aranta,sai ma dadi datakeji domin ta san duk wannan bambamin Fadan dayake Dadi ne yaji yamai yawa Shine yake borin kunya bayaso ya Fada,Harta Fito daga bayin da Rarrafe tafito tayi sallah kafin ta koma ta kwanta tana Sauke Numfashi,ammh azahirin batu taciyu iya ciyuwa wajen Saleem,kasanta ma bata iya hadeshi saboda azaba.. ******************* Saleem shima barcin gajiya ne ya kwasheshi sakamakon jiya bai sami barci na,saboda jarabar Zahra,sai da Malika ta kirashi awaya tana sanar dashi goggo Hadiza da zulai Sun Shirya zasu tafi,shi yatadashi ya Fito daga dakin yazo,ya daukesu acikin motarshi zuwa tasha suka hau mota zuwa Malumfashi,yayi musu godiya sosai kafin yayi musu alherin da zai musu ya juyo ya dawo gida. Gabadaya malika takasa gane kan Saleem don daya dawo dakinta ya Shiga ya dinga barci kamar wani matacce,azahar da la'asar ma gameshi yayi lokaci daya,sai kuma alokacin yaci abinci,zahra ko,ko kofar dakinta bata Fito ba,Abincinta daga na Safe har Rana joda ne,tashigar mata dashi,wacce ke dunkule cikin bargo tana Jinyar kanta,Abunda ya bata tsoro ganin daren Ranar Saleem ya dawo mata irin na Jiya,haka Zahra ke kuka tana rokonshi ammh yaki Sauraranta,domin yana jin kamar manadigosu ne kejansa game da zahra,Sakamon shan magungunar mata da Zahra tayi kafin satinta ya Fita sai da ta gane Shayi Ruwane madara ake samai yayi kauri. Kafin Satin ta rame ta lalace kamar ba Zahra ba Saboda wahala,daka ganta duk tayi Zuru zuru kamar wacce take amai da guduwa,Gashi kullum cikin gashin kanta take,saboda yadda Saleem ya maidata,kuka ko da Nadama tayishi kamar ba gobe,ammh Saleem bai ragamata ba,sai ranar daya gama bakwai dinshi ya koma dakin Malika,kuma Abun mamaki dasukayi Making love da Malika bai Wuce akidarsa ba,lafiya lau komai ya Gudana,Shiyasa gwara ka tsaya inda Allah ya ijiyeka da kaje kana ma kanka jaye jayen banza wanda baida amfani,daya gama kwana biyunshi yakoma dakin Zahra da kanshi ya iza keyarta ta Fito da duka sauran magungunar matan datazo dashi,abun yakusa bashi tsoro ganin irin Abunda Zahra ke dirkama kanta,shi ya Fita da mgungunar ya jefar abola yana tir da masu hali irin na Zahra,bai sauraramata ba,sai da ya tabbatar da Nadamarta kuma tayi mai alkawarin bazata kara shan wani mgani ba,wanda ya Wuce ka'ida,to lokacin ya dagamata kafa,kuma ya taimakamata ta kula da kanta,don ba laifi ta zazzagu har sai da ya kaita wani priver hopt aka bata mganunguna tazo tana sha tana kara Shiga ruwan zafi,sai ga Zahra duk Rawan kafanta,kan Saleem yanzu ta dainashi,ada batajin tsoronshi ammh yanzu dataji muryanshi sai gabanta ya Fadi,domin ba laifi taji maza,ballatana yayi mata mgana jikinta na Rawa zaki ga ta mike duk bai kara waiwaryata ba sai da ta warke ammh tsoron Abun ya darsu aranta,kuma Abunda da zai baka mamaki,duk surutun Zahra ko Nadira bata gayama Abunda ya Faru ba,taja bakinta tayi shuru kada ayi mata dariya. __________________ Kwana bibbiyu sukeyi atsakaninsu Ranar da Malika keda girki joda ce keyi,Ranar da Zahra keda miji kuma ita ke girkinta da kanta,don daga malika har joda ko kallo basu isheta ba,wani lokacin sai dai in sun hadu afalo ita malika ta gaisheta,ammh zahra sai kiga ta amsa a wulakance,Wani abu mamaki in tana da miji Malika bata isa ta zauna afalo ba,don Shige da Ficen zahra cike da gayyah da kuma nuna isa,Ba laifi ta iya girki Tunda momi bata barsu sun zauna a sangarce ba,shiko yanzu Saleem aiki yayi mai yawa baya Wuni agida Sai dare yake dawowa kuma daya dawo ya gaji sai barci gari na wayewa 7 ya fita daga gida,wani lokacin in bai dakin Malika sai dai ya Tuntubeta ta waya su gaisa yaji kodawani damuwa Abunda Zahra kema Malika ya Wuce misali,domin in zahra na Falo tana kallo babu wanda ya isa yazo yadau Remot din ya chanza tasha yanzu zai ga hayaniya da bala'i,shiyasa malika in taga zahra na Falon batama Fitowa Joda ce ke Fitowa tace bamai hanata Fitowa Falo ta gaji da zaman daki,kai ko kichen take tana aikin da zarar Joda ta Shigo zata ce Ta fita,ta bari in ranar girkin uwargijiyanta ta Shigo,Malika ke kwaban joda ammh da yanzu Sun raba hali saboda Abun na Zahra yafara batama Joda rai gaskiya. Hardai wata rana data bangaje Malika har sai ta kusa Fadi,Allah ya taimaketa ta dafe kujera gabanta na Fadi take bin zahra da kallo,takan kawai ta Fito daga dakinta ita kuma ta Fito daga kichen zata Shiga dakinta,ita Malika bata ganta ba,ita kuma Zahra ta ganta ammh saboda mugunta da Iskanci ta bangajeta,wanda yakusa joda ta mareta don datayi mata mgana cewa tayi ita malikar bata da ido,da bata ganta ba,Ran joda ya Fadi suka Shiga sa'insa har zahra na mata gorin tana agolanci agidansu Malika kuma tazonan tana cin arziki ita da gidan mijin,wlh ba macen data isa ta hana ta yin yadda taga dama,Ko ita Malikar ma atafin hannunta take,tana jiran Ranar zata Shiga sabgartane wlh sai tayi Nadama. Malika bata bari Joda tayi mgana ba tattarata suka koma daki,tana ba Joda hakuri tare da Nuna mata kada ta biyema Zahra don abokin mutuwa take nema,so take wani Abu ya faru tsakaninsu in Mallam ya dawo tace kece baki da gaskiya,kinga kuma ba dadi ace baraka yafara bullowa daga Barayinmu ki kyaleta mu hayaniya ba aikinmu bane,shiyasa kikaga bana son zama ako'ina sai adakina gudun Fitina. Koda Saleem yadawo Zahra takasa kunne taji ko zata wata mgana bataji ba,duk ranar ko ita kedashi,jin shuru bai mata wani mgana yasa tayi kyafci aranta tana Fadin"Gaskiyan Saleema ce datace ni na kyalesu,da sannu duk zakuji ubanku daga ke har wacce kike zaune don ita.."itako Malika koda Saleem ya shigo da Safe Cikin uniform dinsa yana Sauri zai Fita koda ya tambayeta koda wani damuwa ne,cemai tayi babu,gaisuwan safe sukayi kafin ya sumbaceta abakinta yafice yana Fadin"Sai ya dawo,addu"ar dawowa lafiya tayimai koda ta rakoshi har kofar dakinta sai taga Uwar gayyah zahra ta cakare rike da jakarsa Ta brief case tana wani Mele baki kamar wata mai jiran cas,tana ganinta ta juya takoma ciki tana Dafe cikinta dataji ya juya mata,tana cije baki don ita ko abaya batayi hayaniya ba,balle yanzu datake kan Siradin rayuwa da mutuwa. Tunda Saleem ya Fita Malika bata Fito ba,sai bayan datayi sallar Azahar,ta Fito tadan mike kafa,saboda sun kara kumbura,kuma tun Safe maranta ke ciwo tana dannewa,Ko joda bata bari ta Fahimci haka ba,bata zata haihuwa bane,don saura kwana 2 EDD ta yacika toh bata kawo haihuwa bace,falon babu kowa,shiyasa ta zauna akasa bayan ta saka Filon kujera ta dafe bayanta dashi Rimot ta dauka ta chanza tasha zuwa Arewa,ta iske sun saka wani Film din hausa,mirmishi tayi domin ba laifin zuwanta zamfara yasa tafara kalle kalle wanda ada ba Halinta bane. Zahra ce ta Fito daga daki tana waya har tazo ta takama Malika yatsar kafa ta kuma tsalleta ta zauna bisa kujera tana cigaba da wayarta,jaye kafarta Malika tayi tana sosa inda ta takata cikin wani yanayi ta kalleta,kamar zatayi mgana sai kuma ta Fasa,ta kada kai ta maida hankalinta wajen kallonta,chan taji zahra ta Sheke da dariya tana Fadin"Wane ita,ai ina gayamiki ita da banza duk daya ,darajan cikinta jikinta kadai takeji Honey yasanar dani da zarar ta haihu zai kalata gidansu taje chan sucigaba da zaman Kunci ita da matar ubanta.."Tafada tana watsamata harara ta gefen ido. Gaban Malika ya Fadi tabi zahra da kallo tana mamakin kalamanta,Kanta ya sara tayi jagale tana kallonta,da gaske ne Abunda take fada ko karya ne,bata gama mamaki ba kawai taji an Fizge Filon kujeran data jingina dashi,Tayi Baya ta dafa kujera tana bin zahra da kallon mamaki,itako kallonta batayi ba,sai ma ta dora kafarta kan Filon tana cigaba da lasta Wayarta bayan ta katse kiran. Wani Fushi ya ziyarce Malika cikin kakkausan murya tace"Lafiyanki kuwa..? Me Filon yayi miki dana tare bayana dashi zaki Fizge,naga dai kina da iko dashi nima ina dashi ko..? Wani kallon Uku Saura kwata kafin ta yatsina Fuska tana Fadin"Nafiki iko dashi Tunda duk inda matar so take itace yar gaban koshin megida.."Tafada tana daga zaune,Wani iri Malika datayi nan da nan hawaye suka ciko mata ido,ta dade tana kallon Zahra kafin kawai ta kada kai ta dafa kujera ta mike dakyar tana Share hanci,Ganin haka yasa zahra ta saka dariya tana Fadin"Ikon Allah jimin mace toh ke in banda Abunki meye Abun damuwa,keda kika ga rashin so zahiri,ai ba babban Tozarci sai mijinka ya sakeka adaren Da'aka Daura maka aure bayan yayimaka fatafata,meyafi wannan Wulakanci,kuma wai mutum saboda dakikanci yana zaton haryanzu ana Sonshi ne.."Tafada tana kara saka dariya. Cak malika ta tsaya tana jin wani kuka na taso mata daga kasan rai,juyowa tayi tana kallon Zahra kafin tace"Duk wa yagaya miki wannnan mganaganun dakike jifani dashi..?"Bude Zahra tayi kafin ta mike tana Rike kugu tace"jiki da wata mgana,wazai gayamin banda honey,Tunda shi aka cuta aka tilastama sai ya maidake dakinki,ke in ma zaki daina rawan kafa ki daina wai ke gaki uwargida bayan da bakinshi ya Fadamin tsausayinki yake babu Uwa asali mai kyau Tunda dangin Arna ne,uba kuma anyi Sanadiyar Shekawarsa da bakinciki,kinga ko ai inda imani ke abun atsausayane ga kuma ciki kinga sai ajira ki haife kafin kiyi gaba.."Tafada kai tsaye tana kallonta. Malika dataji wani abu ya daki kirjinta ya gangaro har zuwa cikinta da maranta bata iya maidama Zahra da amsa ba ta dafe cikinta tana Cije baki cike da azaba lokaci daya hawaye na wanke mata Fuska,wata Shewa zahra ta saka kafin tace"Ji munafukar mata daga mgana sai ki dafe ciki kina kuka,Toh ni kam ban tabaki ba balle ace zan kashe rai.."Tafada kafin tayi tsaki tayi Wucewarta daki, Malika taji hawaye suna zubomata basa yankewa ga maranta daya kulle cikinta na juyawa tama kasa daga kafa,tana kuka ta cije baki tana salatin cikin wannan Halin Joda ta Fito ta isketa cikin Tashin hankali ta isa gareta tana rikota take Fadin"innalillahi Anty malika,meya sameki,haihuwar ce..? Bata iya mata mgana ba,saboda wani azaba daya Turnikota dafa joda tayi tana Sauke numfashi lokaci daya da kuka dakyar ta iya Furta"Ki ki..Kira maman Abba joda inaga haihuwar ce tazo.."Tafada tana cije baki,da sauri joda tatashi ta Shiga daki ta dauko wayan Malika ta kira Maman Abba ta sanar da ita,ita kuma tace tana asibitin yanzu haka,ammh gatan zuwa,kafin ta iso joda ta hada komai na haihuwan datazo sai su Koma asibitin tare dasu,aiko da hanzari joda ta Bude karamin akwatin Malika ta rinka jidan kayan haihuwanta tana sakawa aciki,kafin ta kulle ta zari hijabinta da hanzari ta kinkimo akwatin zuwa falo,koda ta Fito Malika ba yarda take,domin sai mukurkusi take tana kuka,Rikota Joda tayi tana mata sannu kafin tace"Na kira Maman Abba tace gatan zuwa mu je asibiti ko na kira Ya Saleem ne na sanar dashi.."Duk tana halin ciwo sai da ta girgiza mata kai alamun karta kirashi,rike joda tayi kawai tana nishi sama sama ga zufar datake ta Ketomata Malika girgiza kai kawai takeyi tana Tunanin kila ita kan tata ta kare,Sannu kawai Joda ke jerama,ammh ina batama jinta banda Sharban hawaye da Cije cijen baki babu Abunda takeyi,.. Acikin wannan Halin zahra ta sake Fitowa ta tarar dasu,kallon banza ta bisu dashi ganin Malika na wash wash tana zufa yasa ta rike baki tana yar Dariya tace"Topha Abun yazo ne..."Tafada cike da izgilanci,daga Malikar har Joda ba wanda ya kulata kichen ta Shiga ta dauko Tazo tazauna Afalo tana Sha hankalinta,kwance saima Rimot din Tibi data dauka ta chanza tasha,zuwa wata wacce ake wakokin Turanci harda kure Volume tana bi tana karkada kafa. Maman Abba ce ta Shigo ahankalinta tashe ganin halin da Malika ke ciki ne yasa ta rude ta kamota tana Fadin"Kamota joda,haihuwace.."Riketa sukayi har zuwa motar Maman Abba suka sata abaya,kafin Joda ta koma ta dauko akwatin kayan haihuwan da wayarta data Malika,Zahra na zaune bisa kujera tana jijjiga kafa suka Fice daga gidan zuwa Asibiti ********************* Saleem bai da masaniyar Abunda yafaru sakamakon yayi busy ko wayar dayake ma malika ma yau din kwata kwata bai samu yimata ba,har ya dawo gida wajen after 8,dayake zahra keda girki bayan yayi wanka ya sauya kaya zuwa jallabiya,sai ya Fito Falo ta Fitomai da abinci ta durkusa tana cikin Serving dinshi kenan ya kalli barayin dakin Malika yana wani nazari kafin ya kalli Zahra yana Fadin"Ina Malika,tana lafiya dai ko? don Tunda na dawo banji Duriyarta ba daga ita har Joda.." Tabe baki Zahra tayi Daidai tana ijiyemai Filet din Tuwon shinkafan agabanshi tace"Bansani ba,nida naga wannan Nurse din ta shigo sun Fita da ita da Sauri,kamar dai kila haihuwan ce tazo..."Wani uban Zaro ido Saleem yayi yana Fadin"What.."!Haihuwa fa kikace zahra..? Kallonsa tayi cike da mamaki tana Fadin"Eh nake ganin kila haihuwan ne,nifa bansani ba don ba wacce tamin mgana da zasu Fita.." Bai tsaya sauraranta ba,yasaka kafa yayi Fatali da kololin dake gabanshi ya mike yana Fadin"Ammuh ban taba ganin dabba Yarinya irinki ba yanzu ace Malika tafara nakuda har wata makociya tazo ta dauketa zuwa asibiti ki kasa kirana ki sanar dani,ammh don jakanki da rainin hankali har na dawo gida nayi wanka baki sanar dani ba,sai da ma na tambayeki,kuma kina sanar dani mganar banza.."Yafada yana Huci,mikewa tayi tana kallonshi,yadda yake kallonta kamar ya Rufeta da duka,bai tsaya sauraranta ba ya tureta tatafi ta Fadi bisa kujera yawuce dakinsa da gudu ya dauko wayarsa da makullin mota ya Fice da gudu yana cigaba da latsa wayar tasa. _Godiya da Fatan Alheri gareku yan Gidan Amana na *MALIKA MALIK PAID GROUP*..,Hakika kirkinku gareni sai dai nace Alhamdulilah,Allah nake roko ya dafa muku kamar yadda nima kuka Dafamin,Allah ya saka muku da alheri ina godiya Sosai da duka tarin alherinku gareni...Allah yabiyaku da aljannah Firdausi Ameen_😘🙏 *Mommyn ladingo..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 *26* ""Wayar Malika yake ta kira,ammh kuma gashi tana Ringing ammh kuma ba"a picking hankalinshi in yayi Dubu ya tashi,haka ya shiga cikin mota yayi zaune yana dafe kai,wayarsa ne ta dau Tsuwa yana dubawa yaga Wata Nombace agaggauce ya daga kiran yana Fadin"Hello..." Joda dagachan bangaren tace"Hello ya Saleem Joda ce.."Jikinsa na rawa ya Fito daga motan yana Fadin"Joda,kuna ina ne,ina ita malikan? ta haihu ne? ko bata haihuwa ba..? Haka ya Shiga jeramata tambayoyi alokaci daya,cikin damuwa da alhini tace"Muna asibitin da Maman Abba ke aiki,kuma haryanzu Anty malikan bata haihuwa ba,sau biyu ana Saka mata Ruwan Nakuda,ammah haihuwar shuru,wlh Ya Saleem Anty malika tana Shan Wuya,yanzu hakama ana cukun cukun Turamu General hospital gusau ne.." Dafe kai Saleem yayi yana Fadin"Innalillahi wa'inna Alaihirraju'un,ganin nan zuwa yanzu..."Yafada yana katse kiran ko cikin gida bai koma ba ya Fada mota ya tasheta asukwane,da Sauri ya dinga latsama Megadi hon,wanda ya Rugo da gudu ya Budemai get ya sulala zuwa waje da Gudu. ******* Zahra ko tana zaune kan kujeran Da Saleem ya tureta bata iya tashi ba saboda takaichi da bakinciki,tana jin sanda yayi hon da kuma Ficewarsa lokaci daya,tsaki taja afali kafin tatashi tana tattara kololin daya watsar tana Fadin"Allah sa daga haihuwar ta mutu,basai naga karyan Tsiya ba.. ko Ajikinta bata damu ba,saima gyara zama datayi afalo tana chanje chanjen tasha ko ajikinta,saboda gulma ita ta kira Saleem tana Sanar da ita Abunda ya Faru,da kuma halin da'ake ciki,shewa Saleema tayi kafin tace"Kin min Daidai ta wajena,haka nakeson ki rika yin komai cikin taku,ni Allah yasa ma wajen haihuwar daga ita har Abunda ke cikin nata su Haura chan,sai mu fatan Allah ya kiyaye hanya mu sai munzo.."Dariya suka Sheke dashi atare kafin Zahra tace"Kamar kin Shiga Raina haka nace,...."nan suka cigaba da hiransu suna zagin malika da fatan kada Allah yasa ta haihu lafiya,su Fatan mutuwa suke mata,saboda yadda sukaji jininta arayuwarsu ta Duniya. ******** Koda Saleem ya isa asibitin har anbasu takardan izinin tafiya da malika Zuwa general hospital gusai so bai tsaya ba,suka sanyata amota Shida Joda da Maman Abba,wacce ta bar motarta anan asibitin BAyan ta kira Baban Abba ta sanar dashi Abunda ke Faruwa,yakuma amince taje har chan general hospital gusau din. Saleem yayi gudu bisa hanya,sakamakon ganin irin kuka da salatin da Malika keyi tana Fadin ita mutuwa zatayi,duk inda hankalinshi yake toh alokacin atashe yake,gudu kawai yake tsulawa cikin lokaci sai gasu acikin haraban general din,maman Abba ita tafita ta gudu ta sanar Da Nurses su kuma suka zo da Gadon daukan marasa lafiya,ko kafin su kariso sai suka Hadu da Saleem ya daukota ahannunshi nan suka nuna mai dakin da zai Shiga da ita,nan ya Shiga da ita ya kwantar da ita kan wani karamin gado yana kallon Fuskarta yarda halittarta ta chanza Saboda wahala. Korarshi sukayi waje,ammh da ya zauna kusa da itane ya rikemata hannu yana Lallashinta,Ranar dagashi har maman Abba da Joda babu wanda ya Runtsa saboda tashin hankali,har wajen asuba malika shuru bata haihuwa ba,ga karfinta ya kare,kawai sai likitoci Suka Nemi Saleem daya saka hannu zasu Shiga da ita dakin Tiyata,nan da nan ko ya rattaba hankalinshi tashe,daman ya gaji da wahalar da Malika kesha hakanan.. Sai bayan an Shiga da ita dakin Tiyata din ne yasamu sukunin kiran Abbi ya sanar dashi Abunda ke Faruwa,wanda yadinga salati yana kiran Sunan Allah,Koda yake sanar dasu Ummi da hajiya,wacce bata dade da dawowa daga kumo ba,don ko bikin Zahra da Saleem da akayi batanan,Suma salatin suka saka suna Fatan Allah ya sauketa lafiya,itako Saleema tanaji ammh sai ta nuna kamar bata sani ba,nan ko cikin ranta addu'a take kada Allah yasa Malikan ma ta rayu. Joda kuma ta kira Hajiya Binta ta sanar da ita Abunda ke Faruwa,matukar tsausaya Hajiya ta tsausayama Malika,saboda tasani yau zataji Abunda kowacce uwa taji kafin ta haihu,Haka ta dinga mata addu'ar Allah yasa ayi aiki lafiya afito lafiya. **************** Alhamdulillah Anyi Nasarar Yima Malika aiki kuma an Fito mata da kyakyawan yarinyarta wacce take kama da ubanta sak,sai dai ta debo hasken Fatan mamanta,Tuni har ankaisu dakin hutu malika bata Farfado ba,ammh an gyare bby tas gwanin ban sha'awa,Murna wajen Saleem ba'a mgana sai da yayi Sujjuda ya mika godiyarsa ga Allah (SWA) domin Shine ke badawa kuma Shike Hanawa. . Shi yayi ta kiran yan"uwa da abokan arziki yana sanar dasu anfito da malika lafiya kuma ansamu Babby girl,ciki harda Zahra wanda haihuwar kwata kwata bata mata dadi ba,sai ta nunama Saleem din don daya gayamata haka tayi Shuru taki mgana sai da yakara maimaitamata kana tace Allah ya raya ta yanke kiran,ya dade yana kallon wayar yana mamakin zahra yana so ya Fahimci wani abu game da yarinyar,wacce Tun Abunda tayi jiya ya gane ya bar Shiri Tun rani,ammh zai tambayi malika in takoma gida yaji wani irin zama suke gudawar ita da Zahra. Malika bata Farfado ba sai da yammah,nan ta ci karo da Abunda aka Ciro mata,haka ta dauki yarinyar tana kuka,ba kukan komai take ba,sai kukan Mallam zai rabu da ita,acikin wannan Halin ya Shigo ya sameta nan ya hadasu ita da Bbyn ya Rumgume yana mata godiya,ammh abun mamaki Malika kanzil batace mai ba Tun yana ganin Rudin haihuwace da kuma aikin dake jikinta,ammh har washegari Batamai mgana ba,dayayimata zata kauda kai tana kuka Abun yabashi mamaki matuka,ammh sai ya kyaleta sai sun koma gida yaji meya faru kuma. Sai Ranar yakoma Zamfara yabar Maman Abba da joda,koda ya koma Zahra kota tambayeshi ya maijego da bby,kuma koda yake chan Asibitin koda kuskure bata taba kiranshi taji ya ake ciki ba,sai dai inshine ya kirata,mamakinta kawai yakeyi,ammh sai bai mata mgana ba ya kyaleta yaga iya gudun Ruwanta,Ranar bai koma asibitin ba,saboda goggo Hadiza aka turo tazo daga Malunfashi don ta zauna da malika tana kula da ita,tunda dai joda yarinyace bazata iya ba,Maman Abba kuma ta dawo gida,washe garin ma kiran Ummi ya samu yana wajen aiki ta sanar dashi gasu asibitin basu ganshi ba,yace yana tafe,daga wajen aiki gusau din yakoma chan ya tarar da Ummi da Hajiya da Abbi sunce sunma dade da zuwa,sai wajen la'asar kana sukayi Shirin Tafiya inda Ummi taja Saleem gefe tana Tambayanshi"Ina abokiyar zaman malika da batazo asibiti ba,kuma joda ta sanar da ita makociyar Malika ce tazo ta taimakamata kwanansu biyu tare,bata tafi ba sai da goggon Malika tazo..? Kame kame Yafarama Ummi Tundaganan tagane akwai mtsala,kafin yasamu karyar cemata zahran itama tana gida bata da lafiya,Ajiyar zuciya Ummi ta sauke kafin tace"gaskiya Abun baiyi tsari ba ka gyara zamantakewar gidanka,ai yakamata Tunda ba kwance take ba,ta biyoka yau tazo dubata ko? kansa na kasa yace ma Ummi ba daga gida yake ba,ammh insha Allahu gobe zasu zo tare,Ummi bata komai ba,sukayi musu sallama suka koma hanyar Abuja,su suka kawomusu kwando guda na coolers,cike da abinci sai kayan Fruits. Mganar da Ummi tayima Saleem ta tsayamai arai har yakoma gida yana auna magarta inda yaga tabbas gaskiya ne,kuma Duniya na nan na Zaginshi akan Abunda Zahra tayi,ammh ba komai bari Malikan ta daawo gida zaiji dalili,Tun adaren ya sanar da Zahra cewa gobe zasu je asibiti da ita ta Duba malika,kodaga yanayin yadda tayi ya Fahimci batayi niyyar zuwa ba,aiko hakane gari na wayewa Zahra ta kwanta tana rawan sanyi tace bata da lafiya,mamakinta ya kamashi bai mata mgana ba ya sakai ya Fice,wanda duk Abunda tayi Saleema ce ta kitsa matashi,yana Fita ko ta kirata suna Dariya,nan Saleema ke sanar da ita gobe zata zo,su cigaba daga inda suka tsaya murna ta kama zahra tadinga Jin dadin zuwan Saleeman agobe. Har Washegarin Ranar da Saleema zatazo Saleem bai sani ba,saboda Tun Safe yatafi gusau saboda yau din za"a sallamosu su dawo gida,koda yaje shiyayi cike cike da kuma biyan kudin wasu magungunar daba'a biya ba,kafin abasu sallama,shida kanshi yazo yana hada musu kayansu bayan su joda sun kwashi wasu kayan zuwa mota,Nan ne Malika ta kalleshi kafin tacemai tana neman wata alfarma ne,koda ya bata dama kawai sai tace don Allah yayimata alfarma barin ayi suna kafin ya saketa.."Mganar tazomai abazata zama yayi kusa da ita yana tambayanta shi bai gane ina ta dosa ba? waye yace mata Shi Saleem zai saketa..? kin amsashi tayi yayi mganar Duniyar taki magana daga bayama sai ta sakamai kuka,dole ya rabu da ita,ammh bawai don ya bar mganar ba,sai da yayi Shuru ne sai sun koma gida ya turketa yaji daga ina aka samo wannan iskancin. Suna dawowa sukaci karo da Saleema ta iso,Saleem har ga Allah yayi mamakin ganinta,daya tambayeta meya kawota kuma yaushe tazo..? Sai tace bata dade ba,kuma tazo ganin mejego ne da kuma bby,Cikin mamaki yake tambayanta meyasa bata zo asibitin ba,sai tayi missing step tace wai Zahra tace mata yau zasu dawo gida,Yayi mamakin jin haka sabida ko zahra batasan yau za"a sallamo Malika daga asibiti ba? toh waya gaya mata..?bai maida mganar Serious ba,ya share kawai bai zauna ba yakoma wajen Aikinsa,itakuma goggo Hadiza ta saka Ruwan zafi tatara malika bayi tamata wanka ta gasata sosai duk ko achan asibitin tana gasata,ita kuma maman Abba ita tama bby wanka aka sanyata cikin kayan sanyi masu kyau da ban Sha"awa.." Zahra ko Da Saleema wannan Haihuwa dai bata yi musu dadi ba,Har yammah basu shigo sun duba Maijego ba,kuma anajin dariyansu afalo,ammh kuma basu shiga ba,sai dare kana suka Shiga suka dauki yarinyar awulakance har zahra na Fadin tabiyo jar Fatan kakaninta Arna,Tafada tana dariya Saleema ko Fadi take,sai dai amata fatan Shiriya kinsan ana tsotson Iskanci da rashin tarbiya ajikin Nonon uwa.."haka sukayita fadar maganganu son ransu,Joda taso tayi mgana Ammh goggo Hadiza ta hanasu tace su kyalesu komai zasuyi kada su tankansu saboda su neman wanda zai tankasu ne suyi fada dashi,Haka akayi ba wanda ke bi takansu aiki ko ko changal basayi acikin gidan alhalin Saleema cewa tayi zatazo ta taimakama zahra da aiki,Joda ce da Maman Abba ke ta dawainiya da Malika suyi girki su gyara gida,su sakama malika Ruwan wanka,aikin goggo Hadiza kawai Yima Malika wanka da kula da ita ita da Bby,wacce ta samu Ruwan Nono sosai wanda yake taimaka jaririyar wajen samun Abinci sosai. Saleem baida masaniyar Abunda ke Faruwa,don baya zama agidan in yafita Tun safe sai dare yake dawowa,kuma babu wanda ya Sanar dashi ga Abunda ke Faruwa,wanda Wuni suke suna zaune afalo suna Hiransu suna dariya,ko ajikinsu kuma adafa abasu suci suna wulakanci,Malika ko tana cikin damuwa bata cikin natsuwarta saboda ita harga Allah Ta yarda da mganar Zahra tana cikin Fargaban in Mallam ya saketa ya zata kare da rayuwarta,ammh ta gagara fadama kowa ta bar Abun acikin ranta. ***************** Ranar bakwai din na zagayowa Ranar akayi suna jaririya taci sunan Ummi Aisha suna kiranta AYDA,Anyi sha'anin cikin Farinciki da murna,yan malumfashi sunzo harda yan Kumo ma sunzo ansha suna,wanda Su joda sukayi abinci kala kala agidan maman Abba,sun dafa white rice da Miyar nama,sai friede rice da Kuma jallof mai Cosslow,sai Soyayyan Naman kaji dana rago,Sunyi kunun aya,Sai alale na leda,wanda yaji kwai,kuma bayan lemukan da Saleem yasa aka sauke musu domin baki,Kuma su kadai sukayi duka aikinsu agidan Maman Abba,sai dai suka kwaso su cikin manyan kololi suka dawo dashi nan gidan Malika ta Shiga ta Fita cikin kayan alfarma ita da Ayda,musamman maman Abba ta sake kiran Ummi mai lalle da kitso ta sake cakareta,bayan nan mai kwalliya tazo itama ta tsantsaramata kwalliya Abun sai wanda yagani,dayake simple make up ne tayi mata,sai ta Fito ras da ita,Abunka ga farar fata,dama gata da kyau ai sai kawai tashiga kyalli,Zahra ko da Saleema kamar su mutu saboda bakinciki domin ko sun sani wlh karfin hali kawai suke,ammh Malika tafi karfinsu dukkansu,domin ta Wuce da saninsu ta bangarori dama,Ranar sai ga Hajiya saratu momi da Nadira sun diro sunan wanda suka zo suna ta ma zahra Fadan bata sanar dasu malika ta haihu ba,nan tayi ta borin kunya tana Fadin wai ta kira wayarsu bata samesu ba,Nadira ce tace sunyi waya da Saleem yake sanar da ita jiya,yace kuma yau ne Suna,shine ta Fadama momi suka taho,duk da basu wani dade ba,ammh ko malika da basa shiri da zahra taji dadin zuwansu da zasu tafi momi ta bata 10k da kuma Atamfa guda biyu da kayan babys,ko Saleem basu gani ba,don Tun safe ya Fice sakon gaisuwa kadai sukabari agaya mishi. Taron sunan baiyi wasu jama'a sosai ba,daga yan malumfashi ne sai yan kumo,wadanda suma suna gama cin suna suka koma,dama sunzo da motar gidane,sai yan group din *MALIKA MALIK PAID* Da yan *HAFNAN AND JANAF PAID GROUP* Da sukayi mata kara mota guda suka zo ma malika sunan Ayda wanda ta dinga mamakin daga ina suka samu lbrinta,nan Dotata Ladingo tayi dariya kafin tace"Karki damu da sanin ina muka samu lbrinki,domin mommyna Janafty ita take sanar damu lbrinki,kuma dukkanmu nan masoyanki ne,duk dabamu taba ganinki ba,muna kaunarki.."Jin haka yasa malika tayi murna sosai da Farinciki nan aka zubo musu abinci suka baje suna ci suna hira,su Sisina Aisha alto da Sahiba sai ci ake hannu baka hannu kwarya😂su mommyn Abdul me,su Rafi'atu,Fati sadi,mommyna khadija tame gari,momyna khadija bashir,Dijah Abdul,Dija muhd,Zuwaira Andijat,My besty halima,Fatima zahra,haleema,Ummi imran, Mmn useey,Ummi bilal,Fatima garba,mom sadiq,Suwaiba,shafa yola,Murja bagudu,Deejart,Mmn baraka,Mmn Amira,mm siyama,Ummu bilal2,Rouky niger,Azeeza,hadiza,Durling Rukayyah, Masoyiya takwarar malika,khadija Aliyu,khadee Noor,mmn Haneef,Mmn mama,yar Fulani,Nazeeha Ahmed,Saleema Hamza,Ayshert usman,Maman khairat,Bbyj,Asma'u Shehu,Ummah sabo,Zainab jega,Hafsart Umar,Fatima musa mamn Nabila,Mmn ummulos,Nafeesa Fee,jikar hajiya,Mrs Umar Faruk,Sardiya,Suna da dayawa wanda bakina bazai ya ambatonsu duka ba. Sunsha Ankonsu cikin red din materila sunyi head da blue,abun sai wanda ya gani,malika tayi Farinciki ganinsu sosai haka sukayi ta daukan Hotuna suda malika da bby Ayda,Fatima zahra ko ana riketa tana abarta ta Shiga dakin Zahra taci ubanta😂🤔Dakyar Su Nazeeha da Ummi imran suka rirriketa suna bata baki kana ta hakura,Har sukayima Malika sallama bayan sun bata sha tara na arzikin da suka kawomata ,basu saka Zahra da Saleema a ido ba,ammh d Yawansu sun so su gansu koda tsaraban Harara ne su basu koda bazasu dake su ba,Saboda murna da godiya har bakin mota joda da Malika suka rakosu suna musu godiya suna dagama musu hannu har suka Fice daga gidan.😂 Anyi taro lafiya an watse taro,Ayda da mamanta sunyi goshi matuka domin Abbi 50k ya aikomata dashi Ummi ko akwati tayi Sir da kayan Babby da mamanta balle dataji ita akama takwara,Ya marwan ko Shima kayan yara ya turo dashi daga lagos,da kudi 30k akabama malika,haka shima Sadiq kudi yabata 20k Malika saboda Farinciki sai da tayi kwallah ta kira Abbi da Ummi tana musu godiya tana kuka,harta da Sadiq din da Marwan Saleem ya kirasu yabata tayi musu godiya sukace ai babu komai suma yarsu ce,Su Zahra da Saleema ba karamin mamaki sukayi ba da sukaji uban Dukiya da kayan da malika tatara,nan da nan hassada da haushi ya kamasu,nan Zahra taji itama tana son ta samu ciki itama ta haihu ataramata kudi,Niko nace banza abanza,ke keta Dukiya indai kudi ne Malika ta mallakeshi da wanda zai siyeki keda Mai zugakin gabadaya. Shiko Uban gayyar bai siyan mata komai ba,illah wata sarkan gold mai kyau Sarka da Dankunne,Ranar daya kirata ya damkamata sarkan adakinshi ne,yana rike da Ayda ita kuma malika na Faman gwada sarkan gaban madubi tana washe baki murna ta cikata Fadi take"Wayyo Mallam wht a special gift,gaskiya am so hppy wlh Allah ya saka da alheri ya kuma rayamana Ayda cikin tafarkin islama.."Da Ameen ya amsa yana mata dariya Abun yayimai dadi yadda ta nuna murnanta afili,domin yasan cewa Malika ta mallki dubunsu kafin yanzu kuma ko ayanzu tana da Dubunsu ammh kalli yadda take murna akan kyautan da yayimata wacce bata Wuce yarwa abola ba indai awajentane.. Kwantar da Ayda yayi bisa gado ya taso yazo ta bayanta ya Rumgumeta duka kyakyaawan Fuskokinsu suka bayyana acikin madubi,mirmishi take sakin mai bayan ta dora hannuwanta kan nashi,cikin wani salo yayi mata Rada akunne yana Fadin"Ummi Ayda.."yafada yana Shinshinar Wuyanta Cikin kasalar daya saukarmata tace"Umhmm Abbu Ayda.."Mirmishi yayi har Hakoransa farare suka bayyana,Cikinta ya mtsana tayi yar ihu tana Fadin"Kai mallam wajen operation din nefa ka tabamin.."Tafada cike da Shagwaba Saurin juyo da ita yayi yana Fadin"Ayyh am srry.."Ya fada yana shafa kumatunta,Kafin yace"Tambayarki zanyi,kuma ina so ki sanar dani gaskiyan al'amarin.." Hannayenta ta harde bisa kirji tana Fadin"yes ina jinka,Allah yasa na sani.."Gyara Tsayuwa yayi yana kallon cikin kwayan idanunta Yace"Mganar dakikamin a asibiti kince kada na sakeki sai mun dawo gida? waya sanar dake cewa nace zan sake ki bayan kin haihu..? Shuru tayi tana dukar dakai taki mgana,Ganin tayi Shuru taki mgana yasa yace"Kinga ki sanar dani waya gaya miki wannan mganar da bata da Tushe ballatana makama,in baki gayamin ba,zan kira goggo Hadiza yanzu,kila ita in ta tambayeki ki sanar da ita.." Jin haka yasa ta riko hannunshi da Sauri wanda yake Shirin Fita,bisa gefen gado suka zauna kafin tace"Basai ka sanar da kowa ba,Bani son Tun bayan daidaitan al'amarinmu babu wanda ya sakejin kanmu kai baka alfahari da hakan..? kai ya gyada mata bai yi mgana ba,Sai tacigaba da cewa"Toh meyasa zaka kai karata? dama zan sanar dakai Wacce ta Fadamin ammh sai kamin alqawarin bazaka dau wani mataki ba,kowani hukunci ba.."zuru yayi mata da ido yana kallonta kafin yace'Banyi alqawarin ba,ammh ki fara sanar dani Abunda ya Faru..", Hannunshi ta riko ta matse cikin nata kafin ta fara bashi lbrin Abunda yafaru da ita da Zahra ranar,bata rage komai ba ta karishe cikin kuka tana Fadin",Na shiga tashin hankali Mallam,wlh in ka barni banson ya rayuwata zata kare ba,ga Shi Daddy ya tafi ya barni bani da kowa sai kai,kai ne gatana,don Allah kada ka barni ka zauna dani koda bazaka kyautatamin ba,kazama bango Abun jingina gareni.."Tafada tana Fadawa bisa kirjinsa tana kuka. Riketa yayi yana buga bayanta,idanuwansa sun kala sunyi jawur,Sai yanzu yake kara Fahimtar Abubuwan da Zahra ta aikata Tun haihuwar malikan,Ashe munafukace Mai Fuska biyu,kuma gulman nata harda mijinta aciki,lalle yazama Dole yayi gaggawan daukan mataki akan Zahra kuma sai ta sanar dashi wajen wa taji wannan mganr,Cikin sauri ya raba Malika da jikinsa ya mike yana Wuce ya Fice daga dakin atamanin,cikin Tsoro Malika tabishi tana Fadin"Mallam,tsaya kaji..Ka tsaya..."Tafada tana kokarin Fita sai kukan Ayda ya dakatar da ita ta koma da hanzari ta daukota ta sabata,ta bi bayan Saleem da Sauri. Tundaga Falo ya ke kiran Sunan Zahra murya a kaukaushe.."Zahra!.Zahra..! Zahra...Zahra..."!Yake Fada yana Bude murya cikin bacin rai,Zahra da Saleema dake kan gadon Zahra suna hira sukaji muryan Saleem yana kiran zahra cikin muryan bacin rai,atare suka diro daga kan gadon suna Rigen Rigen Fitowa daga dakin,Ba su kadai ba hatta joda dake cikin daki ita da goggo Hadiza suka Fito hankalinsu tashe,saboda jin kiran bana lafiya bane. Zai Shiga dakin Zahran kenan sai gata tafito agaba Saleema na biye da ita,Tana Fadin"Lafiya hone...."Ji kake Tas!Tas!Tas!...."Saleem ya kwashe Zahra da maruka Zafafa guda uku atare,saboda gigita da zafin mari sai da Zahra ta wuntsila tayi baya zata Fadi Saleema ta tarota ta Fado jikinta,cike da mamaki suke binshi da kallo yadda yake nuna Zahra da yatsa yana Sakin Huci,daidai lokacin da Malika ta kariso idanuwanta duka awaje saboda karan marukan dataji zahra tasha.... *Am srry yau baiyi yawa ba,wlh Tun jiya Typing din ke bani mtsala,har sai da nayi kwallar😭,dakyar da Sidin goshi ta yarda na karisa muku wannan,so in kukaji Shuru kawai kuyi hakuri sai na kaita an dubata...*😭😭😭😭😭😰😰😰😰🙏🙏👏👏👏 *Mommyn ladingo..,"* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘 _Littafin *MALIKA MALIK* Na kudi ne ki biya kudin karatu akan Naira 200kachal👌ki turo ta account Nomba kamar haka 0552179550 *JAMILA UMAR GTB* bayan kin dauki hoton Sreenshoot din Transaction  din,sai ki turomin ta wannan Nombar 09069067488,Ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488 shima kai tsaye bayan an dauki  hoton katin sai aturo*_     *27*        "Yana Nunata da yatsa cikin Fushi ya Furta"Ashe haka kike Zahra bansani ba,agidan Uban wa na gayamiki zan saki Malika in ta haihu..? Yaushe na taba tattauna wannan mganar dake don Ubanki..? Yafada yana kwalalo mata ido,..    Daga Zahran har Saleema atare jikinsu ya Fara rawa,Zahra na Dafe da kunci lokaci daya hawaye suka wanke mata Fuska ganin irin Tozarcin da Saleem yayi mata agaban kishiya da yan"uwanta harda zaginta,ganin haka yasa ta jajige Razanarta ta mike ga kanta tana Fadin"Eh mana kazo da borin kunyama Tunda kaga gaban matarkace? in ba kai ka gayamin ba wazai Fadamin ba,ko kasheni zakayi bazan Fasa fadan kai ka gayamin baka Son Malika ba, Baka kaunarta,kai cemin ma kayi baka Kaunar mai kaunar...."Jikake Tim.."!Zahra ta Fadi akasa,wanda Saleem yasa kafanshi ya kwasheta zuwa kasa,kafin ya fara kokarin kwancen belt din wandon Jeans din dake jikinsa cikin Zafin rai da Zuciya yake Fadin. "Ba malika ne baniso ba,kece bantaba kauna ba Zahra,kuma yau zan tabbatar miki da cewa Na tsaneki...!.."Yafada yana kwanto belt din Malika ce ta mikama Joda Ayda ta isa gareshi tana Riko hannunshi take Fadin"Plz mallam A'a kada kafara ba mutumcinka bane,juz leave her,ka barta da Halinta.."Fizge hannunshi yayi har sai da Malika ta kusa Faduwa ko,sai da tayi da gaske,ta iya tsayuwa bisa kafafunta dakyau.   Bai Saurari Malika ba,ya shiga Tsulama Zahra belt din ba ji,ba gani yana Fadin"Zaki fadamin waya gayamiki kokuwa haryanzu kina kan bakanki.."Yake Fada yana Shimfidamata belt din ta ko'ina,Itako Tun tana Dauriya Harta Saki baki tana ihu da kuka,Joda ko sai dariya take ranta yayi mata Dadi,Malika ce idanuwanta ya cika da kwallah don ita bata saba ganin Tashin Hankali ba,Wajen goggo Hadiza ta nufa Tana jan hannunta take Fadin"Goggo don Allah ki saka baki,kiba mallam Hakuri don Allah ya bar dukannta.."Goggo Hadiza tace"Ki rabu dashi Yanzu ko nayi mai mgana baji zai yi ba,kema kiyi Shuru da Bakinki.." Dole Malika tayi Shuru tana Raba ido itako Saleema jikinta ne yakara Daukan mazari saboda tsoro ta Rakube jikin bango tana rawan sanyi da makyaryarta tana Tsoron kada Zahra taji duka tace abakinta taji,ai tasan yau kwananta ya kare,itako Zahra ganin zai mata illah ne yasa ta Rike belt din da hannuwanta duka biyu tana kuka take Fadin"Wlh ba kai ka Fadamin ba,zan Fada...!Zan Fada wlh..."Take Fada tana kuka kamar wacce ake zare Ranta,. Idanuwanshi Jawur,yace mata"Ki yi hanzari sanar dani wani munafikin algumgumin ne ya sanar dake wannan mganar,har kike jifan Matata uwar ya'ya da ita,ki sanar dani Wanene ko wacece...? Ya Fada cikin Tsawa Zahra na Sosa gefen kunnenta inda Belt ya sameta,😂kallon Saleema take wacce ke girgiza mata kai alamar karta Fada,ganin haka yasa Saleem ya Ware ido yana kallon Saleema yana Fadin"Au kece Don Ubanki..."?Yafada cikin Tsawa da Tambaya yana nuna ta da belt din dake hannunshi. Saleema ta fara ja da baya tana mannewa jikin bango take Fadin"A...A ..A'a Bani bace fa..."Take Fada har idonta ya ciko da kwallah,ganin haka yasa Zahra tayi Saurin Cewa"Wlh ita ta Fadamin,ita ma tace Wai bakason Malikan wai..Wai...Wai...Kuma.." wai Kuma me..? Ya katseta cikin Tsawa yana kwalolo mata ido,ganin haka yasa Zahra tace"Wai ba don Allah ka maida Malika dakinta ba,sai don kudin mahaifinta,,(Karya ta karama Saleema,don so take yarda aka jifgeta toh ayima Saleema mafiyinshi domin duk Abunda ya Faru itace Sila.) Baki Saleem yakama cike da bakinciki da mamaki yake bin Saleema da wani mugun kallo,itako jin Abunda Zahra ta Fada yasa tafara mgana tana hawaye "Wlh karya takemin Yaya,ban gayamata haka ba,sharri ta kullamin wlh Allah.."Tafada tana kara matse jikinta,nan ko Zahra tahau Rantse rantse tana Fadin Saleema ta gayamata,sai kaji tashin zencen Zahra bata rage duk makircin da Saleema ke kitsamata ba harda karya ta kara,saboda tana so aci uban Saleema dakyau sosai,Zahra harda Sanar dashi Saleema tazo ne,don su hadu su Fitar da malika daga gidan.." Ba Saleem kadai ba hatta Su joda sai suka rike baki suna mamakin Saleema,shiko Saleem nufarta yayi yana mirmishin takaichi yake Fadin"Saleema kanwata..Hmmm,umh..."Yake Fada yana Nufota ganin haka yasa ta nemi guduwa taku daya yayi ya Rikota,Ai sai ta zame tana so tana bashi hakuri tana kuka,wuyan Rigar Atamfanta dama ya riko,ai bai tsayawa wasa ba ya Shiga tafkan Saleema kamar Allah ya aikoshi,Malika tayi kokarin Cetonta,ammh saboda yadda Ranshi ya baci ko gani bayayi har sai daya sameta ahannu tayi baya tana sosa wajen,Ganin haka yasa joda tace"Don Allah Anty malika ki bari yaci ubanta,ai wlh tayi Abun duka haba,dan'uwanta Fa.."Goggo Hadiza bata yi mgana ba sai da taga ya kai Saleema kwance yana duka kafin ya hadasu ita da Zahra ya cigaba da tafkansu atare,dkyar ya saurari goggo Hadiza ta karbi belt din dake hannunshi ammh bayan ta bari sun lallasu,domin sun jiki kowannensu jikinsu duk shatin belt ya kwanta kuka suke kamar ransu zai Fita. Yana huci da Numfarfashi yake Fadin"Saleema,Zahra dukkanku Babu Abunda zence muku sai nagode da sakayyar ku gareni,kunyi ikirarin zaku kori Malika daga gidan daku kukazo kuka tarar da ita,to Alhamdulilah kafin ku koreta ku bari ku Farayin gaba,Zahra wlh nayi nadamar Aurenki saboda haka kije na SAKEKI SAKI DAYA,..."Malika ta kwalalo ido,goggo Hadiza ko Fadi take"Assha Ashha..Saleem hukunci yayi Tsauri.." Hannu ya daga yana Fadin"goggo kibarni,wlh aurenta ya Fice daga kaina,dama kuma kadarrace ta sani aurenta bawai don ina jinta acikin zuciyata ba.."Yafada yana huci Zahra ko hannun ta daura bisa kai tana Fadin"Wayyo Allah na Shiga uku ni Zahra Fatima,don Allah honey kamin rai kada ka rabu dani.."Take Fada tana kuka,tsaki yaja kafin yace"Dallah Rufema mutane baki sakarya Wawiya kawai,ke har kina da bakin yima malika gori akan bana Sonta,kin ma san miye so,Toh bari na gayamuku Abunda banta gayama kowa ba,ko gabanki kike wankewa kibani wlh bazaki kamo mtsayin malika acikin Raina ba,in kince zaki kishi da ita,sai dai ki mutu wlh don bazaki taba samun mtsayin data samu ba,saboda haka ki tararra ina inaki kibarmin gida ki koma gidanku ki kuma Sanar da iyayenki wajen Gudirin koran kishiyane Reshe ya juye da mujiya,ke kuma..."Yace yana nuna Saleema da hannu. "Kin kyauta in kuma nuna min Cewa kedin kin Fita Dabam acikin ya'yan Ummi da Abbi,shegiya mai Fuskar alade ki rasa inda zaki zo kiyi munafuncinko da gulma sai gidan Dan"uwanki harkina bada goyon bayan ayima matar dan"uwanki wulakanci Saboda mugun Halinki,baki Tunanin kema wata rana gidan wani zaki,ko don kina ganin Sadiq bai da kanwa baki Tunanin yana da ya'yan yan'uwa..? kema za'ayi miki haka? ya zakiji? ko kuma ayima yar da zaki Haifa zaki so..? Amsan ita ce A'a ammh kuma kike kokarin cima wata Zarafi agidan Mijinta,wlh Saleema Tir da munanan Halinki kema ki tararra kayanki ki barmin gida yanzu ba sai anjuma,kuma yanzu zan kira Ummi da Abbi na sanar dasu Abunda kika aikata,in kin koma chan ma kikara amsan hukuncinki,Dabba kawai wacce batasan nata ba.."Yafada yana Shureta da kafa kafin ya juya afusace ya Shige dakin yana banko kofa Ranshi bace kamar Zuciyarsa zata Fito waje.   Malika ce tabi bayanshi Da Sauri tana zuwa jikin kofa tajita akulle gam,baya ta dawo tana Dafe kai,Joda ko dake Rike da Ayda cikin Towel,ta fara Dariya kamar cikinta zai kulle,Zahra da Saleema da suka ji jiki,suka bita da kallo idanuwansu jajir,kowacce Fuskarta ta chanza Saboda Wuya,Saleema ta fara Ture Zahra wacce ke kan Kafadanta tana kuka,dagowa Zahra tayi tana kallonta cikin bacin Rai take Fadin"Allah ya isa tsakani na dake Saleema,gashinan wajen zugani na Raba Malika da honey ni kin kashemin Aure.."Tsaki Saleema taja Tana mikewa dakyar take Fadin"Allah ya isa ta biki munafuka,daman chan da ra"ayinki na ganki da baki da mugun Nufi akanta dana kawo Shawaran ai ba Dole nayi miki ba ko? Tafada tana mata wani Wulakantattacen kallo,ganin haka yasa Zahra dingisawa ta mike tana cakumo wuyan Zahra tana kuka take Fadin"kece ai munafuka Komin mugun Nufina inda ban samu goyin bayanki ba,da bazan iya yi ni kadai ba,Ammh saboda rainin wayau bayan kin kashemin aure,shine kike Fadamin mgaanar banza,Ran Saleema ya baci ta kalli Zahra tana Fadin"Sakarni don uwarki..."Baki Zahra ta rike tana Fadin"Lalala..Har da zagin Uwata,to anki asakeki din don uwarki kema,Tunda uwa batafi uwa ba.."Jin haka yasa Saleema ta Fizge riganta daga hannun Zahra tana Fadin"Andai ji kunya wlh,Ni sai yanzu nake nadamar biyemiki Domin Tun Farko na gane ke Shashashace.."Tafada tana hararanta kafin ta Shige dakin Zahra tana Sosa bayanta inda belt din ya Shigeta dakyau Kukan kura Zahra tayi tabi bayanta tana Fadin"Kutumar ubanchan To Fitomin daga daki.."Daga cikin dakin Saleema ke bata amsa da Cewa "Dakin ki ko dakin Yaya Saleem,don ko banza ni ina da gado agidan ko yau ya Saleem ya Fadi ya mutu,ke fa.? Saki ne fa akanki kinga ko baki da wani iko da dakin nan.."Nan suka Shiga suna zagin junansu da cin mutumci,Malika ta rike bakwai aranta tana Fadin"Lalle Zamanta zamafara yasa ta Fara karatun Duniya,Joda ko goggo Hadiza daki suka koma suna fadin Allah Shi kyauta,dama Ramin karya kurarrene,kuma dama haduwar abota indai ta munafunce bata karfo,kuma indai tatashi Rabewa bata rabewar arziki. Haka kowacce ta Fito dauke da katon akwatinta da mayafinta bisa kai,har suka Fice daga gidan suna tsiya taku da tona ma juna asiri suna zage zage kamar zasu daki juna,koda suka isa tasha suna tare,kuma da Saleema ta hau motar Abuja,itama Zahra nan ta Shigo nan Saleema ta kalleta tana Fadin"Ke mara Mutumci ina zaki danaga kin Shiga motar Abuja.."? Zahra bata tankata ba Sai da taja mata wani dogon Tsaki kafin tace"Kina da son bata bakikin,aikwai inda zani wanda ya Wuce gidan iyayen Mijina,chan zani muje kowa ya maimata Abunda ya aikata nabama Ummi hakuri na Roketa ta Roki Honey ya maidani dakina,don ni dai ko giyan wake nasha bazan koma gida ba.."Baki Saleema ta bude kafin tace"Bazan taba bari ki koma gidan Ya Saleem ba Zahra,domin dama chan baki dace da yayana ba Malikar dai itace ajinsa..."Baki Zahra ta mele kafin tace"Daga baya kenan,wai anyi Sadaka da karuwa,kanki kuma akeji yanzu.."Tafada tana juyama mata keya,har mota tatashi suna Tsiya har sai da wata mata dake ciki ta musu mgana kana suka Saurara. Shiko Saleem dama yana Shiga dakinsa Bayan ya kulle kansa,bai kira Ummi ba sai da fushinsa ya Fara sauka kana ya kira Ummi yana gayamata Abunda ke Faruwa kamar yayi kwallah,Ummi da Ranta ya gama baci da jin Abunda Zahra ta aikata kuma Abun haushi harda Diyarta Saleema cikin Fushi da takaichi tace"Ina Fatan kaci uban Shegiya ka barta kwance ko,...?"Yace"Nadai mata hukunci Ummi buh ita Zahran na Saketa gaskiya Ummi,bazan iya zama da ita ba wlh.."tsaki Ummi taja kafin tace"To waya kwasota ai ni dama Tun ranar dana Fara ganin idon yarinyarnan nasan akwai zence,Allah ya kyauta in ta yi hankali sai kadawo da Matarka.."Shuru kawai yayima Sukaci gaba da mgana,nan yake Tambayanta Abbi don yace ya kira Nombarshi bata,nan take sanar dashi yana meeting da Shugaban kasa,sun dade suna mgana da Ummi kafin kowanne ya yanke kiran. Da Ummi take Fadama Hajiya Abunda ya Faru mamaki da Haushin Saleema ya kamata,tayi ta sababi ita kadai,harta Fadin bari kabirun ya dawo azo ayi mganar aurenta kawai Da Yaron nan Sadiq,tun bata da mutumci,Zuwa yammah kuwa sai ga Zahra da Saleema sun Diro,Ummi takaichi kamar ya kasheta,ganin yadda Zahran ke kukan munafunci,ko dayake bata ga laifin Zahra ba,babu babban mai laifin irin Saleema,Ummi tayi Fada kamar ta daketa,haka Hajiya babba Ta nuna mata abunda tayi Rashin kishin kanta ne,domin har Abada Saleem dan"uwanta ne,Dakin dai Saleeman Zahra ta sauka,ammh ko mgana basu ma juna,Ummi tace ta jirata zuwa gobe suyi mgana da Abbi,Abbi koda yadawo Ummi ta sanar Shuru yayi yana maimaita Sunan Saleema,Ummi ya sa ta kira masa Saleeman yayi mata Fafata yaci Mutumcinta sosai kuma yace maza ta Shirya kayanta a Asibitin Mallam Aminu kano zatayi Housemanship dinta,Saleema tayi kuka da Nadamar dama bata aikata Abunda ta aikata ba hakuri tayi tabama Abbi,ammh yace wlh chan zata,kuma mganar aurensu da Sadiq kwananan zata tashi,bazai zura mata ido tana bin gidan Dan"uwanta tana Assasa rashin zaman lafiya atsakanin matanshi ba.    Ummi ko datayimai mganar yasa baki Saleem ya maida Zahra dakinta,kiyawa Abbi yayi yace mata dama Tun mganar Auren Zahra ya yayi alqawarin bazai kara shiga Sha"anin gidan Saleem,ta barshi shima magidancine,kuma hukunci da yayanke Shine Daidai gareta,ganin haka yasa Ummi ta nemi izininshi gobe in ta dawo daga court don tana da wata Shari'a zata saka Zahra agaba ta maidata Zamfara,Tunda ta nuna tayi Nadama,Bai damu ba yace adawo lafiya. ************** Saleem bai saki Fuskarshi ba sai da gari ya waye kana ya fara warwarewa,ammh itama malikan tasha Fada,Akan meyasa in Zahra tayimata wani Abun bata sanar dashi,toh meye amfanin ta amtsayinta na Uwargida,kuma yayimata Fushin yadda ta nemi ta yarda da kalaman Zahra na cewa zai saketa,ya sanar da ita in har zai saketa ai ba Tsoronta yakeji ba dabai Fadamata ba,Ita dai Malika nata ban hakuri da kuma mai alqawarin insha Allahu haka bazata kara Faruwa ba,bai saki ba Fuska Sosai don Ranar ko breafast baiyi ba ya Fice zuwa wajen aiki,Ranta duk ba Dadi don bata son wannan Saleem din nata tafison Abu Ayda na yanzu yafi dadin zama da Dadin Sha'ani.     Dukkansu basu san da Zuwan Ummi ba,sai gashi wajen karfe 1 sai ga Ummi da Direba tazo tare Da Zahra,haka Malika ke rawan jikin Tarban Ummi,ita kuma tana Fadin tazo ta zauna jego take,Sai bayan su gaggaisa ne da Malika da goggo Hadiza da Joda,Tunda tazo Ayda na rike a hannunta Zahra na gefe ta rabe kamar wata mutuniyar kirki da akwatunta agabanta,Ummi ce ta tambayi Saleem,Malika tace yana wajen aiki,waya Ummi ta Fito dashi ta kirashi tace yazo gata agidanshi tana jiransa yanzu zata Tafi ne,bai jima ba sai gashi yazo Fuskarshi ta kara Dinkewane lokacin daya cikaro da Zahra,cogewa yayi yaki zama yana Fadin"Ummi dama wannan munafukar gida taje,ke Abuja nan ne gidanku da zaki tafka hauka miji ya sakeki kuma kije chan.? ya Fada yana kallon Zahra cike da Tsana. Ummi ce ta dakatar dashi Da Fadin"Saleem zo ka zauna bani son Shanshancin naka.."Jin haka yasa yazo yazauna akasa akusa da ita yana gaisheta,ganin haka sai Malika tatashi zata Shiga ciki,sai Ummi ta kirata ta dawo ta Umarceta data zauna domin mganar ta Shafesu dukkansu ne,dama Joda da goggo Hadiza tunda suka gaisa da Ummi suka koma daki,Kafin Ummi tafara mgana sai data fara Rokon malika gafara bisa Abunda Salema da Zahra suka aikata gareta,Kusan Malikar Taku da Sanyin Hali nan da nan ta yafe musu dama bata Rikesu ba,Ummi taji dadin haka harsai da Ta nuna afuskarta,Bangaren Saleem kuwa sai da Ummi ta Fitomai a uwa sak kana ya yarda ya yafema Zahra har ya maidata dakinta,ammh ya gayama Ummi da Sharadi wlh tallahi last chance ya bata in takara duka Sakin biyu zai cikasa mata,Nan Ummi ta yarda bayan ta sa Zahra ta duka tabama Saleem hakuri,shi kuma yace bazai hakura sai inda Ta Roki malika ta yafemata tukunnah,don ita suka batamawa,Dole Zahra tabama Malika hakuri ba don Ranta yaso ba,sai don Tsira da Aurenta datake matukar So,malika batayi gaddama ba tace ita bata taba kallonta da wani Abu ba,taje ta Yafemata,Ummi taji dadi sosai nan ta tarasu tana ta yi musu Nasihan zama lafiya da Hakuri da juna,kafin daga karshe tayi ta sakama Malika da Saleem albarka tana bayyana yadda suke alfahari dasu. Ummi bata tafi ba sai datayi la'asar ammh kafin tatafi sai da takara jan kunnam Zahra sosai,ta nuna mata taji kuma insha Allahu itama zata zama mace tagari kamar Malika,Ummi kuma dazata tafi ta Shiga har dakin Malika ta damkama wani Abu abakar leda tace zata kirata awaya ta mata bayani karba Malika tayi tana ma Ummi godiya,Dole Ummi ta ijye Ayda wacce take nanike da ita Tunda tazo ammh tadaukan ma Abbi sabuwar Amayarshi hotuna,don ta kara Nunamai yadda Ayda takara girma,har bakin mota suka rakata ita da malika suna dagamata hannu har motarsu ta Fice Daga get din gidan. Suna tsaye Saleem ya juya zai koma cikin gida Malika ta riko hannunshi tana kallonshi bai kalleta ba,sai ma wani hade rai dayakeyi,Matse hannunshi tayi tana Fadin"Maraba da Uwa ta gari gaakiya Ummi tayi Abunda kowacce uwa ta dace tayi,naji dadin yadda ta dawo da Zahra dama harga Allah banji dadin Hukuncin daka yanke ba.."Wani kallo yayi mata kafin ya Rike hannun data Rike shi dashi yana Fadin"Uhm ke murna ma kikeyi ko? kinsa me,ma Umarni zan baki ba Shawara ba,ni nasan zahra ba Tuban gaskiya tayi ba,duk Randa ta sake Miki gori ko wata mganar banza ki daki bakinta sai yayi jini kafin ni nazo nayi mata mai dalili.."Baki ta rike tana yar dariya tace"Wane ni? Ka Rufamin Asiri ,Insha Allahuma bazata kara ba."Jinjina kai yayi kafin sufara Taku zuwa cikin gida,. Mirmishi Malika keyi kafin tace"Mallam yaushe zamu dora daga karatunmu.."Bai kalleta ba yace"Duk Ranar da Ummi Ayda ta Shirya toh Abu Ayda Shima ashirye yake.."Dariya tayi tana kallonshi kafin tace"Na tambayeka...? Yana kallonta ya dagamata kai,Idanuwanta na cikin nashi tace"Da gaske ne,Abunda ka Fadama Saleema da Zahra..? Gira ya dagamata kafin yace"Me...? bata Dauke idanuwanta akanshi ba tace"Kana SONA....? Sun dade suna kallon Juna cike da wani yanayi kafin shi ya lumshe ido ya bude yana Fadin"Nan ba wajen da zamuyi wannan mganar bane kibari kigama wannan jegon Tukunnah.."Yafada yana jan karan hancinta,batayi mgana ba,illah kanta data aza bisa kafadanshi,shikuma ya sako da hannunshi guda daya ya Rumgumeta yana Sakin Ajiyar Zuciya,ji yake kamar ya maidata cikinshi saboda yadda Zuciyarsa ke bugawa Saboda ita. Saleema ko kwana biyu takara Abbi ya Tarkatata ta koma Kano cikin Asibiti inda zatayi Housemanship dinta,Saleema taji kunya Sosai saboda harda ya marwan Sai da ya kirata ya mata Fatata,ya zageta kamar ya fito ta wayar yaci ubanta haka yakeji,Kuka ta sakaimai tana bashi hakuri,yace bashi zata ba Hakuri ba,Malika da Saleem zata bama hakuri,haka ko akayi Ummi ta Turamata Nombar Malika ta kirata ta bata Hakuri malika tace ta yafemata wlh. Shiko Uban gayyar sai da ta kwana2 tana kiranshi bai dauka ba,sai ana uku kana ya dauka,Saleema na kuka tana bashi hakuri tare da alqawarin tayi Nadama kuma bazata kara ba,Bai hakura ba sai da ta sanar dashi takira Malika ta bata hakuri kana ya hakura har sukayi mgana tace tana kano,Nasiha yayi mata na ta maida hankali kan karatu kafin suyi sallama,shiko Sadiq dayaji lbri wajen Ya marwan Takakkiya yayima Saleema har kano ya nuna mata tayi Wauta,Saleema dai Tashiga uku kowa ganin laifinta yake,Nadama ko tayishi ba adadin Tayi Nadamar Abunda ta aikata,daga karshe Goge Nombar Zahran tayi acikin wayarta ma gabadaya ta maida hankalinta kan Abunda ya kawota. ******************* *AFTER SOME DAYS*   Zahra ta chanza kamar ba ita ba,yanzu babu Rawan kan nan ko kadan,domin shikanshi Saleem din bai Fara kulata da cin abincinta ba,sai da ya tabbatar da Nadamarta kana,kuma ya saka mata Dokan dole da Safe ta rinka zuwa tana gaida Malika don Tana gaba da ita. Toh Babu laifi Duk batasaki jikinta ba,ammh zata bita har daki ta gaisheta ta dauki Ayda ta mata wasa,ta gaida Goggo Hadiza tayi Fito,joda ma sukan gaisa in suka hadu,ammh ba sosai ba don ita Joda har yanzu gani take Zahra nada Sauran wani Abu Ranta,domin ko Fuskarta ka kallah zaka ga bata Fara'a Sosai.   Malika bata tsaya wasa ba tacigaba da karatunta wajen Malaminta ,gefe daya ga kuma girkin datakoyo domin Tunkafin ta haihu dama ta iya wasu,saboda Shiga kichen din datakeyi tana ganin yadda Joda keyi,Shiyasa ta zage Damtse kafin Joda tatafi ta samu ta koyi wanin Abu,kuma ba laifi tana da kwalkwala komai daukeshi takeyi,Ga kuma Shirin Akushi da Rufi na Arewa baya Wuceta shima tana karuwa dashi sosai,Maman Abba bata son da wannan kalmar zata gode mata ba,domin taba Rayuwarta dukkan wata gudummuwa,shiyasa ta hadamata Turamen Atamfa masu kyau da Tsada guda biyar da Kuma kudi gefe daya ga Naman suna data dibanta da yawa wanda dama su sukayi wahalanshi harta mutanen Kumo da Malumfashi sai da aka aika musu dashi,harda yan group din Malika malik paid da kuma Hafnan and Janaf paid group suma kowa ya samu kasonshi😂,Maman Abba kin karba tayi Sai da goggo Hadiza ta saka baki kana ta karba tana godiya sosai.   **************** Ana Saura kwana biyu Malika tayi arba'in Sai ga wayar Hajiya binta ta kira Saleem da kanta inda take sanar dashi Ranar Asabar mai zuwa alkalin alkalai mai ci ayanzu zai raba gadon Dukiyar Daddy so duka Manajojin kamfanoninsa dana gidajen mansa anyi musu waya zasu tararra komai suzo dashi harda Mrs suzan wanda suke Da Rubutattacen komai na hannayen Jarin Da daddy ke dashi akasashen ketare so za'a hadu Ranar asabar din domin saukema Daddy Nauyi kuma malika ita kadaice yar'shi kwara daya daya mallaka,shine zasu zo shi da ita,da sauran yan'uwanshi da suka rage daga Malumfashi domin gani da ido.. Da Saleem ya gayama Malika ranar Mutuwar Daddy takara tasoma Malika tayi ta kuka Yana lallashinta,Dakyar ya samu tayi Shuru,dama kuma Abun yazo adaidai domin goggo Hadiza zata koma malunfashi itama Joda zata tafi,shiyasa suka Shirya Tafiya alokaci daya Malika da Joda da goggo Hadiza Tun Ranar Jumma'a Tasaka Direba yazo daga gida ya daukesu ya kaisu katsina Shikuma Saleem sai gobe zai zo Saboda Ranar yana da meeting,Ammh yama joda da goggo Hadiza sha tara na arziki suka karba suna godiya. Rabon Malika da gidansu Tun bayan Tafiyarta lokacin Rasuwar Daddy,lokacin data Shiga gidan sai da tayi kuka domin tana ganin kamar Daddy zai Fito yace"Bbyna..."Ammh kuma Daddy yatafi Tafiya ta har Abada,Hajiya ta dauke Ayda tana cillata sama tana Bangala mata Dariya,ita mamakin girma Ayda take kamar wata diyar Turawa,Goggo Hadiza tace ta samu Nono mai kyau ne Shiyasa,Malika ko tazo da kayanta dayawa Tunda Mallam yace zata kwana biyu har Abuja zata gidansu ta kwana biyu kafin takoma Zamfara,shiyasa harda guzurin mganin matan da Ummi ta kawomata tazo dashi domin tafara amfani dashi,don Ummi ta kirata ta mata bayanin gumba ce,da kuma garin aya wanda zata dinga damashi da madara,sai wata hadin zuma wacce zata dinga shanta ita kadai,Ranar Malika sai da tayi hawaye taji aduniya ai batayi maraici ba,balle goggo Hadiza ma bata barta haka ba,kayan Fruit din duk matsa mata sha,take tana da kuma Shan Abu mai Romo romo,ita kanta goggo da Hajiya Sunji dadin yadda Saleem ya yarda zai bar Malika ta kwana biyu in yazo gobe saboda su samu lokacin yimata gyaran da basu yi mata ba lokacin Aurenta. Dose da mery ko nanan Gidansu Malika suna taya hajiya aikace aikace,Suma sunyi murna da ganin Malika,haka suke rigen rigen daukan Ayda har suna Fada,malika ko na musu Dariya cike da Nishadi **************** Zahra ko tana ganin Su Malika sun Tafi ta Fito Falo ta Fada kan kujera tana Fadin"Gida yazama nawa ni kadai,hakama miji yazama nawa nikadai,ammh da wannan matar ta gaje komai,wlh bantaba kaunar Malika ba,kuma bazan taba kaunarta ba..,Kawai nayi lambo ne abubuwa su yi sauki kafin na Fito da wani sabon salon.."    _Akwai wan lbri dake Tsungulina,Lbrin ba irin Salon da kuka sani bane,Salo ne da zai karkata kan wani al'amari dake cimin Tuwo akwarya na Yadda Mata take mallake Miji ta rabashi da kowa nashi ciki harda Uwar data Haifeshi..? Bayan ta rabashi da kowa nashi,sai yakoma nata da ita yan'uwanta..? Shin yaya Abun zai kasance..,..? Sai kun yi jimarin bina sannu a hankali mun gama malika da aminci in Allah yaso,sai mu Dora cikin wannan Lbrin nawa wanda zai zo da Sabon salo..._ *Mommyn ladingo..*   *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *ƖŊTҼɭɭƖƓҼŊT WɾƖTҼɾى ASSɷ📚* *_Mallakar:Janafty_*😘    *28* ""Saleem sai washegari da Safe yazo,inda aka hadu aka Raba gadon Tarin Dukiyar Daddy,wanda Malika ta samu kaso mafi rinjaye da tsoka domin kusan rabi da kwatan Dukiyar natane,Hajiya ma ta samu nata kason,Sakamakon Dady bashi da uwa ba Uba,kuma ba wani dan'uwa da suke Daki daya ko kuma yan Uba duka Babu wanda zai iya gadanshi bayan Malika da hajiya,sai kuma cikin kawunan Daddy akwai wadanda suka Shigo cikin magada. Anan Hajiya take Sanar da Malika cewa Zata koma Malumfashi ita Joda,tunda gidan da suke ciki malika ta gajeshi,ai nan da nan Malika tace batasan wannan Zencen ba,Tace Har Abada hajiya bazata bar gidan ba,zata cigaba da zama tare dasu merry ita zata cigaba da biyansu,kana manajojin Kamfanonin Malika tayi mgana dasu Tace su Cigaba da gudanar da komai sai lokaci bayan lokaci zasu dinga mgana ta waya,hannayen Jarin Daddy na kasashen ketare kuwa an Dawo dasu ne an rabasu,tsabar kudin da Malika ta mallaka banda kamfanoni bata san iyaka ba,shiyasa kuma bada cigiyar Filaye inda tace tana so agina islamiya,da masallaci,domin sadakatul jariya zuwa ga Daddy. Hakika wannan bayanin nata ta saka Farinciki azuciyar kowa,mussaman Mijinta Saleem wanda Farincikinsa yakasa boyuwa har sai da ya bayyana mata,bai koma Zamfara ba aranar sai awashegari ammh yammah nayi yace Malika ta Shirya tazo suje yawon bude ido😂Tako cakare ita da Ayda Suna Fita bai su zame ko'ina ba sai gidansu wanda Daddy ya basu,Allah sarki megadi na nan da wani wanda yake kula da gidan,komai yana nan amuhallinsa babu Abunda ya chanza.   Malika tasha mamakin ganin hatta cikin dakunan tsaf tsaf,ashe Hajiya ta kansa merry da Dose suzo su gyara lokaci bayan lokaci,basuyi masauki ako'ina ba,sai akan gadon Da Saleem ya karbi budurcin Malika haka ya Rumgumeta kam idanuwansa alumshe yake Tambayanta.."Kin Tuna wannan gadon Ummu Ayda.."Cikin kasala ta dagamai kai bai bata zarafin mgana yace"Toh wannan gadon shi yakafa miki tarihin zama azuciyata wanda baki Fita ba,kuma bazaki Fita ba har Duniya ta tashi.."Kuramai ido tayi cike da mamaki tana kallonshi bai bata xarafin mgana ba,sai da ya tsotse lebunanta kafin ya hada dogayen hamcinsu waje daya yana Fadin'Tun Ranar dana aikata miki wannan Abun,ban kara Sukuni ba,tunda lokacin Ashe sonki ya Shigeni sai nake dauka Tsausayinki nakeji sai daga baya na Fahimci na Fada acikin kogin sonki wanda baida iyaka,Wlh Malika zuciyata tanayin Xafi matukar na ganki cikin damuwa,kukanki tamkar zubowar dalma daga zuciyata,Bata miki rai kuwa tamkar Nima an batamin ne,Bana samun sukunin zuciyata sai naji gangar jikina ta hadu danaki..Yau na Na sanar dake Abunda na boye miki I SO MUCH LOVE U MALIKA..."Ya Fadamata idanuwansa na chanza launi. Kamkameshi Malika tayi tana hawaye Da dariya lokaci daya,Kanta takara tusawa bisa kirjinsa tana Fadin"Bani da bakin mika godiyata gareka,domin asanadin Abun ka min akan gadon nan,ya chanza rayuwata na dawo malika datace na dawo mace kamar kowa,har Abada kai Abun alfahari na ne,Duk Abunda kamin bai hana zuciyata ta Fada tarkon sonka,Ina Sonka Abbu Ayda fiye da Yadda nakeson kaina.."Tafada tana dago kanshi bakinta takai kan nashi Tafara tsotsan lebenshi cike da kwarewa shima kan nata ya rike da hannu bibbiyu ya mikamata harshensshi tana cigaba da Kissing dinshi kamar Allah ya aikota shiko gabadaya jikinsa da hannuwanshi rawa suke saboda yadda Malika ke Tafiyarshi dashi cikin Kwarewa. Ayda ko na gefe tana barci,iyayenta ko sun gama rikita juna,cikin xafi zafi Suka raba kansu da kayan jikinsu suna kara Shafa sassan jikin junasu cike da So da kauna,Awannan daren Darene mai cike da tarihi wanda Malika da Saleem bazasu manta dashi ba,darene daya kunshi tarihi kala kala,sun gudanar da wata rayuwa mai tsayawa azuciyr masoya,haka Saleem ya kwana yana jadaddama Malika kalmar yana Sonta,tagani kuma ta yaba domin ya nunamata a aikace haka Saleem ya tasata lasheta daga sama har kasa,itakuwa ta jiyar dashi madaran dadin daya Kasa controlling kanshi tasha Surutai sai da tagaji Ta rufemai baki. Washegari da Safe tare sukayi wanka su kama Yarsu Ayda kowannensu anan ya chanza kaya Tunda dama Daddy ya siyasu komai,kamar karsu bar gidan haka suke ji,shiyasa Saleem yace zai nemi Transfer adawo dashi Katsina sai su tararra su dawo nan,Malika ko taji dadin haka sosai,sai da suka koma gida yayi Sallama dasu hajiya kana ya Sallame Malika kafin yakama hanyar komawa Zamfara cike da kewar matarsa da soyayyar yarsa Ayda.. ***************    Zahra yanzu ta Sadda kai kasa ne,in kuka ga yadda takema Saleem ladabi da biyayyah sai kun yi mamaki baya mgana kanta na sama sai akasa,kuma kullum cikin makircin tambayanshi take yaushe malika zata dawo..? Tayi kewaar Ayda sosai,sai da yayi mirmishin jin dadin Zahra ta zama mutum yace Suna tafe insha Allah. Ganin haka yasa Saleem ya sakarma Sosai suna baje Soyayyarsu domin Ta nuna itama tana kaunar Malika da Abunda ta haifa baisan ta munafuncin bane,gashi taci riba domin Saleem yanzu yana kokarin bata lokacinsa sosai suna shan love wanda ko lokacin amarcinsu basu sake da juna haka ba. ************ Malika ko sati daya tayi A katsina ta Wuce Malumfashi tayi kwana uku wanda babu Shakka dangin mahaifinta sukaji dadin ganinta ta zaga dangin sosai wanda dama tare da Joda sukaje,dagachan suka Wuce Abuja,Ummi da Abbi kamar su goyata haka suka dinga dawainiya dasu,Ayda ko suna zuwa Abbi ya amsheta suna sama wajensa,Saboda dadin zama agidan Ummi sati daya cur Malika ta kwashe,ada har tana da niyyar karawa Saleem ya kirata awaya yace in takara bada yawunshi ba ta dawo don wlh ya gaji kewarshi zata illatashi,Aiko da Ummi sukaji zata koma aiko tace batasan wannan Zencen ba,sai taje kumo ta dawo kafin ta koma,Ransa baiyi dadi ba da Ummi ta kirashi tana Sanar dashi sai Malika taje kumo ta dawo kana,bashi da yarda zaiyi dole ya hakuri suka tattara suka Tafi kumo duka gidan harda Hajiya,kwana daya sukayi suka dawo Ita kanta Malikan kwana Daya ta kara Direba ya kwasheta ita da Merry Tunda Joda Tun a malumfashi ta barta,shiyasa hajiya tace tazo da merry saboda ta dinga taimakamata da Renon Ayda in ita kuma tana wasu ayyukan,ammh sai da ta kira Saleem ta nemi izininshi baiyi gaddama ba ya amince,Malika bata yi kasa agwiwa ba tazo da System dinta wanda rabin kasuwancin mahafinta keciki,tazo dashi saboda tana so ta Tuntubi Saleem in zai barta ta dinga gudanar da komai tana gida basai taje ba,Tund Gabadaya babu Abunda bata sani akan kasuwancin ba. Saukan yammah sukayi so Saleem baya gida sai Zahra wacce tayi kiba kamar ba ita ba,tadai Fito tayi musu sannu da zuwa daganan tayi komawarta daki Ranta bakikirin Da dawowar Malika wanda ta sani yanzu duk Jin dadin data samu zai rage ne,haka ko akayi don Ranar ko takanta ma Saleem bai bi Tunda ya dawo yana nanike da Malika,Tunda suka Shige daki basu Fito ba Sai Washegari wanda hakan ya kona ma Zahra rai kamar tayi Bindiga saboda kishin Malika balle yanzu dataga tafi da kyau da iya tsara kwalliya komai na Malika mai kyau shiyasa komai ta saka yake mata kyau,bata kwalliya sosai ammh kuma duk kayan data sanya sai sun amsheta,balle Ranar girkinta yazo bata wasa da duk Abunda ya Shafi mijinta,Komai zatayi sa cikin lokaci ne,bangaren girki kuwa Malika bata da mtsala domin ko gane wani Abu ne batayi ba,zata dauki wayarta tayi browsing taga yadda komai yake ta kuma yishi yadda yakamata..   Zumuncinsu da Maman Abba ko yakara kullewa ita ke kara koyamata wasu dabarun zama da miji ammh ita malika Tuni ta samu key din Rayuwar Saleem ahannunshi,Bata mai gaddama kan Abunda ya haneta,koda tana son Abun nan da Zarar yace "A'a to ta barshi har gaban Abada,kuma ko Fuska bazata nuna taji haushi ba,Abu na Biyu bata Raina Abunda yake mata ita da yarta komiye in ya Siyo mata zata karba ta Gode masa sosai yadda kasan ba'a taba mata makamanciyar kyauta irinta ba,Duk da ko tarin Dukiyar da Allah yayi mata bata Raina Abunda mijinta yayi mata,sai Abu na uku Tarbiya Malika bata tsalleki mganarsa tana girmamashi tare da ganin Darajarsa in yace ga hanya tabi nan take saka kai babu gardama gata da Sanin wayewar Duniyar Tafiyar da miji cikin sauki,toh tana da iliminta daidai Gwargwardo to wadannan hallayar ta Kara sace Zuciyar Saleem wanda ko mgana tayi Shima bai iya tsallaketa,kuma yake Fifitata akan kowa duk da yana kokarin kwatatan Adalci Atsakaninsu da Zahra,ammh bata ganin kullum cikin kishi take da kyashi akan Malika da yarta.. Mganar kula da kamfafoninta da suka zama mallakinta kuwa Tun kafin tayimai mganar ya Tuntubeta ya kuma bata dama ta rika gudanar da Komai acikin gida,Tunda ga Na'ura mai kwakwalwa ga waya,Shima yayi mata alqawarin bata dukkan gudummuwanshi Murna wajen Malika ba"a mgana dama ita tana son kasuwanci sosai nan da nan ko tacigaba daga inda ta tsaya rabonta da wani Kamfanin daddyta Tun kafin Aurenta da Saleem,yanzu kuma saboda karfin gwiwanshi da Soyayyarshi gareta ta fara Dawowa Ainihin Malika malik dinta,ammh wannan ba Wacce kuka sani abaya bane,ta yanzu She very smart and Educated both na addini dana boko. Sai ya koma in tana kan Na'ura Merry ke kula da Ayda,ko in tana kichen tana girki Ranar ko da bata da aiki Shikenan ammh merry ta taimakamata sosai Duk da ma Aydan bata da Rigima sosai,Abu daya Fara Tunzura Zahra Shine Soyayyar da Saleem ya kwashe kaso mai yawa yamikama Ayda wanda ko ita matarsa baya Sonta haka,Ko malika kedashi ko ita kedashi yana Nanike da Shegiyar yarinyarnan baya ijiyeta sai dare ya tsala lokacin kwalliyar datayimai Duk tagama goge kanta Saboda Haushi ma tafiyarta dakinta take tayi kwanciyarta sai sanda yagaji da kanshi ya maidama uwarta kana zai zo ya kwanta,wani zubin har ta Fita girki baya Nemanta Saboda daya dawo bashi da Hutu jikinsa na Rawa zai karbeta da ita zaici abinci wanka ne kadai ya ijiyeta in zai Shiga,wannan Abun yanzu Shike damun Zahra sai ma tatarra tsanarta kacokan kan Ayda wacce batafi wata uku Aduniya ba,in ko ya ijiyeta ya Shiga wanka haka Zahra zata dinga Dungurin yarinyar tana hararanta sai taji motsin zai Fito sai ta dauketa tana lallashi kamar gaske,shiko ganin haka sai yaji dadi har yana cemata in taga Malika na aiki ta rinka zuwa tana daukan yafi merry wacce ba musulma ta dinga wahala da ita,sai ta nuna kamar ta Allah harda cemin tana matukar Son Ayda kamar Ranta,shiko har Ga Zuciyarsa yace mata tabari Malika ta sake haihuwa sai su bata,Wani bakin ciki ya cika mata rai wato Malika ne zai karama ciki ta haihu ba ita ba ko? Tundaga lokacin ta dauki damaarar Azabtar da Ayda matukar ta Shigo hannunta,musamman take karbanta  ahannun merry ta Shigo da ita daki ta dinga saka yarinya kuka tana mganarinta tana zaginta,sai gaji da kuka zata maidama Merry ita kuma ta kaima Malika ta bata nono,Wanda zatayi ta mamakin ganin Ayda haka duk tasha kuka Fuskarta tayi jajir,ita da bata da Rigima ko ta tambayi merry sai tace Anty Zahra ce ta karbeta,jin haka yasa Malika bata Shigo da wani Tunani zatayi Saurin kauda Shedan daga Zuciyarta. ***************** Bayan Sati biyu Zahra ta samu waya daga kano cewa An kwantar da momi Hajiya Saratu a asibiti,Dole suka Shirya tafiya harda Malika sukaje suka dubata,ammh su sai ka dawo Saleem yace Zahra ta zauna ta kwana biyu Tunda dama bata taba zuwa ba,ammh afuskar Zahra ya Fahimci bata ji dadin Cewar da yayi zai barta ba,haka ta bata rai har suka Tafi,ita kuma ba komai ne yamata bakinciki ba,sai yadda zata bar Malika da mijinta su kadai agida shine kishi ya Turniketa taji kanon ya Fita aranta,itako la'akari da Momi dake kwance ba lafiya batayi ba,A'a ita hankalinta na gida,Shiyasa Adaddafe tayi kwana hudu ta dawo sai dai suka ganta kwatsam,Saleem yayi mamaki Domin Sati daya yace tayi daya tambaayeta ba'asi sai tace Ai momin ce taji sauki Ita tacema ta taho gidan Mijinta,alhalin ko achan cema Momi tayi ita da Nadira Cewa Saleem ne yace kwana uku yabata ta dawo gida,Abba najin haka ya hadota da Direba ya maidota Zamfara. *Momyn ladingo..*   *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *MALLAKAR*Jamila Umar A.K.A janafty*💕 *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_   *30* ""Shigowar Su Malika ne ya dakatar da Saleem daga,d'aga hannun dayayi zai Naushi Bakin Zahra,wacce ta Sulale kasa tana kuka hannunta Rufe da bakinta tana makyarkyarta. Malika ko Wajen Ayda ta nufa cikin Rawan jiki ta dauketa tana jijjigata batama kai ga Zarafin mgana ba,Taji muryan Saleem cikin wani yanayi yana Fadin"Why..? Zahra me nayi miki..? Me malika ta tsare miki..? Wani alhaKi Yar jaririya Ayda tayi miki da kikeson kasheta.?."Atare joda da Malika suka kwalolo ido suna bin Zahra da kallo Wacce ke girgiza kai tana kuka take Fadin   "Wlh batamin komai,Sharrin Shedan ne,ammh ni ko kuda Bazan iya kashewa ba.."Tafada tana gunjin kuka tana daga hannuwanta,Saleem bai iya mata mgana ba,sai da Numfashinsa ya koma daidai kafin yace"Hakane bakomai,Allah nagani ban Aureki da Wata Zuciya ba zahra,nayi kokarin ki zama mace tagari hakan ya gagara Daga karshema Saboda bakin kishinki kamaki nayi kina neman kashe yar Jaririyar Allah Wacce bata ji ba bata gani ba,ammh ngode ma Allah daya Toni asirinki Tunkafin ki aikata Abunda kika niyya,kije bazan hada ki da hukuma ba,ammh zan Sallameki daga Rayuwata sallama ta har Abada,Saboda haka kije na Sakeki saki biyu kuma Tsakani dake Zahra Allah ya isa,bazan taba yafe..Miki ba.."Yafada kamar kwalla zata zubomai Shiyasa ya Fice Daga dakin da Sauri yana Share hanci. Itako Zahra zaman yan bori ta karayi akasa tana kuka hannunta biyu bisa kai tana kururuwa tare da kuka alokaci daya tana Fadin"Wayyo Allah na..!Kaicho na ni Zahra na kashe Aurena dakaina.."Take Fada tana kuka mai hade da Nadama mai karfi,Malika da joda dake tsaye agabanta suka daskare atsaye suna binta da kallon mamaki mai cike da tsoro. Zahra ta rarrafa zara riko Kafar malika,ita kuma tayi Saurin yin baya tana girgiza kai Wasu hawayen Tsausayin kanta dana Yarta na kamata,kara rumgume Ayda tayi tana Fadin"Ban taba Zaton zafin kishinki akaina har yakai kiyi Tunanin kashe Jaririyar da batasan komai ba,haba Zahra me kika Dauki Duniya ne,duk Abunda Zaman lafiya da hakuri bai baki ba,Wlh tallah akasinsa bazai taba baki ba,Meya Rufe miki ido?Dukiya.?ko ko Shikanshi Mijin..? Wanda duka Zaki Mutu ki barsu anan Duniya kije lahira ki girbi Abunda kika Shuka..,Hakika kin bani mamaki Zahra,ammh kuma ngd ma Allah daya Tsaremin Ayda baki riga kin aiwatar da mugun Nufinki akanta,babu Abunda zence miki,tunda kin riga da knga karshenki.."Tafada tana kuka kafin ta sakai ta Fice daga dakin Zahra na kururuwan Kiran Sunanta. Joda ta Shiga Tafa hannu tana fadin"Innalillahi ni joda na Shiga Aljannah,ammh dai kinyi Asara wlh,yanzu ke Zahra ina miki kallon mara hankali Ashe kallon biri nake miki kina min na ayaba,Toh Allah ya Shiryeka yasa wannan Ya zameki Darasi knga dai karshen Wanda yaja da ikon Allah don Malika da Saleem haduwar Allah ce bata ta mutum ba.."Tafada kafin tajamata dogon Tsaki ta Fice, Nan Zahra ta kara Faduwa tana kuka harda birgima Nadama Tare da danasani suka Shigeta lokaci Daya tana Danasanin meyasa ta biyema Sharrin Zuciya Dana Shedan,gashi ya kaita ya baro,yanzu me zatacema iyayenta a auren da ko Shekara bai yi ba..? Bazata iya bude baki ta Furta irin Abubuwan Data aikata Saboda Tasan Halin Abba da momi suma bazasu mata da Wasa Ba. Gajiya Tayi da kukan ganin babu mafita yasa ta tashi ta Shiga hada kayanta amanyan akwatunanta,Sai da ta hada komai nata kana ta koma ta Zauna tana Sharan kwallah,sai ga Saleem ya Shigo saurin mikewa tayi tana mutseke ido zatayi mgana kenan ya Mikamata Farar Takarda hannunta da jikinta na Rawa ta mika hannu ta karba tana kallon Fuskarshi wanda ya kauda kai alamun bayason ganinta ma kwata kwata,Ta karba ya sakai ya Fice ya barta tana zubewa bisa gado Tana Tsiyayan Hawaye. Zahra da kanta ta Dinga jidan akwatunta zuwa waje,megadi ne ya Fita ya samo mata mai Napep ta Shiga Zuwa Tasha inda ta hau motar Kano,har suka kai kano Zahra na kukan Nadama da kaicho da Rayuwarta haka Napep din data Shiga da Inda mota ta Sauketa zuwa,gida nan ma kuka tayi tayi,kuma haka ta Fadama Falon gidansu tana wannan kukan megadin gidansu ne ya Shigo da akwatunta yana Sanar da Momi Mai napep na waje yana jiran kudinsa Momi da ke Falon ita da Nadira suka mike Arazane atare suka Tarbi Zahra suna Tambayanta lafiya bata iya mgana ba illah Takardan da Saleem ya bata ta zaro ta daga cikin karamar jakarta ta mikama Nadira,momi kuma na kokarin ciro kudi cikin pos dinta Dake kan kujeran daya Daga cikin wadanda sukama Falon kwanya 500 ta mikama megadi ammh Rabin Hankalinta naga farar Takardan Da Nadira ke warwarewa tafara karantawa abayyane kamar haka.   _NI *SALEEM KABIR KUMO* Na kara karishe yanke igiya biyun daya Rage a tsakanina da *ZAHRA BUKAR MADA* Sakamakon munanan hallayata wanda in kuka Tambayeta zata Sanar daku da kanta,Ina Rokon Allah in azamana da Zahra na cutar da ita ko na Mintina daya na yarda ku iyayenta ko Rokarmata Allah ya Sakamata,in ko Azamana da ita Ita ta Cutar dani kuyatani Rokon Allah ya sakamin Akanta.._                 _* ACP S.K.Kumo.*._ Daga Nadira har Momin hannu Suka Dora bisa kai suna kiran Sunan Allah da Salati lokaci daya,itako Zahra kasa ta Sulale tana gunjin kuka Momi na kallonta cike da Tashin Allah.."Innalillahi Wa'inna alaihiraju'un Zahra garin ya haka ta Faru,yaushe Mijinki ya sakeki da zai ce ya karishe igiya biyun dake Tsakaninku,yaushe wannan Abun ya faru ammh mu bamu sani ba...? Tafada tana Rike haba cike da damuwa,Itako Zahra taki mgana banda kuka babu Abunda takeyi Haushi yakama Momi takai mata Duka tana Fadin"Don Ubanki bazaki mgana ba..? Mekika aikata har ya sakeki saki biyu lokaci daya,kuma a yadda yaron nan yayi Rubutu Zahra kece kika jama kanki Zawarci da yarintarki,Kinje kinyi Abunda kika kashe kanki kika kuma kashe mu iyayenka,Wlh baki kyautamana ba Zahra.."Take Fada tana kuka Nadira ce ta Rikota tana bata hakuri tana Share mata hawaye,itako zahra kukan ta take karama Volume Saboda bata da karfin gwiwa bada lbrin Abunda ya Faru Momi batayi sanya ba ta Daga waya ta kira Abban Zahra tace ya dawo gida yanzu ba lafiya,jin muryanta cikin wani yanayi yasa ya umarci Direba daya juyo dashi gida,dama yana hanyar Zuwa gidan Wani abokinsa ne,koda yadawo gidan nan ya iske bakin lbri wanda ya kusa saka Zuciyarsa bugawa,yayi tambayan Duniyan nan Zahra taki mgana sai kuka take,daga karshema tashi tayi ta Shige daki Nadira tabi bayanta,ganin haka yasa Abba ya kira Layin Saleem din ammh kuma wayarsa tana kashe,sai ya sauya alaqaan kiran Zuwa ga IGP KABIE KUMO,wanda Shi Abba ne ma ke Sanar dashi Abunda ya Faru don su basu da lbri,ammh yabashi hakuri da janjanta lamarin inda yace zai Nemi Saleem din yaji gaskiyan batu Abbi Ummi ya sanarmawa Abunda Bukar Mada ya kirasa ya sanar dashi kirji ta Dafe tana salallami,wayar Saleem tayi ta kira bata Shiga sai ta kira na Malika,bayan sun gaisa take Tambayanta ina Saleem,wanda lokacin yana dakinsa duk Wunin yau bai ci abinci ba saboda Damuwa da Nadamar Auren Zahra daya lullubeshi Malika tayi ban hakuri ammh yace ta rabu dashi bayason cin komai,Yana kwance akan gadonsa ta mikamasa wayar tana Sanar dashi Ummi na Son mgana dashi karban wayar yayi ya saka akunne alokaci daya yana gaida Ummi bata tsaya amsawa ba ta Shiga jeromai Tambayoyi kan Abunda Bukar Mada ya kira Abbi ya sanar dashi baiyi Nauyi baki ba ya sanar da Ummi duk Abunda ya Faru baki ta rike tana mamakin Zahra,Duk da Zahra tayi Abunda bai kamata ba,ammh Ummi tanuna Saleem yayi kuskuren yanke Hukunci cikin Fushi,ta kuma bashi Umarnin ya kira Mahaifin Zahra yamai bayani don daga mganarsa Zahra taki mgana,ya sanar da ita zai kirashi da Safe,da haka sukayi sallama tana Fadin Allah ya kyauta na gaba Koda ta Sanar da Abbi lbrin da Saleem ya bata tsaki yaja yana Sababin Yarinta kenan da Shigen Rawan kai irin na Saleem,ammh ina shi ina mata biyu,da lokacin da ya Rarito an hanashi ba hanuwa zaiyi ba,ammh yanzu wa gari ya waya..? Allah ya kyauta ammh sam basu da Tunani inda suna dashi da duk haka bata Faru ba,shima Allah ya kyautan yayi toh babu wani gyara Tunda Saki ukun ya cika kemata sai Da Fatan Allah yasa yazama darasi garesu gabadayansu...    Hajiya Babba ko dataji Fada takamayi da saleem din wai meyasa bai bata kashin mutuwa ba kafin ya tarata,Shiko Ya marwan dama yace Daga ganin wannan amaryar ta Acp batajin mgama,Saleem ko sai Washegari ya kira Bukar Mada ya Warwaremai zare da abawa Tundaga Farko har karshe sai gashi Daga karshe Bukar Mada kebama Saleem Hakuri yace babu komai kanta tamawa,koda Hajiya Saratu momi taji batayi wani mamaki ba,don tasan wauta da sakarci irin na Zahra kuma ga Abunda Nadira tace ta kirata tana fada mata,duka Momi ta hada Fadan da kuma Takaichin Zahra ta Watsar illah ta Sanar da ita idai kan kishiya zata kare rayuwarta aiko Tana da Wahala don yanzu Rayuwa ta chanza ba lalle bane mazan yanzu su zauna dakai kai kadai ba,balle keda kika je kika tarar ammh har kina da kokarin Son ki kori ta ciki,wanna Shine kaikayi ya koma kan mashekiya. ***************** Sai bayan kwana biyu kana Saleem ya warware,ranar monday ya Fita office,ammh adaren sunyi Tsiya da Malika kan tacemai ita daya nemi Shawaranta da bai saki Zahra ba,Wanman mganar Shiya batama Saleem Rai har ya Nunama Malika hakan,Dakyar ta bashi hakuri ya hakura ammh ada har ya dau Zafin da Cewa kila ko bata Sonshi ne,da har zata ce ya cigaba da zama da Zahra wacce bata son Jininsa toh aiko bata Sonshi karyan banza ne kawai. Da Maman Abba Taji lbri sai da tayi Guda bayan ta juya Duwawau Tacema Malika ta tayata barka,domin Rabuwa da muguwar kishiya irin Zahra babban nasara ce,wanda zama dasu bala'i ne Tunda Zuciyarsu bata da kyau sam,Toh ita kanta Malika Tasan Zahra ba masoyiyarta bace,ammh sakin ne bai mata dadi ba,shiyasa ko da taga Saleem yasa anfitar da komai dake dakin Zahra an saka Sabbi tsoffin kuma yabama megadi yace yakai ma ilayanshi ya karba yana murna Hade da godiya,Sai merry ta koma tana kwana adakin,joda kuma bata dade ba takoma Katsina wajen Hajiya. ***************** Yanzu gida ya rage daga Malika sai mijinta Saleem sabuwar Soyayyah mai dauke da Sabuwar Rayuwa mai cike da muradi da burgewa nan suka bajema juna yadda suke kaunar junansu,kowa yana kafa kafa da Dan'uwanshi bayason bacin Ransa,gefe daya kuma suna kula da yarsu Ayda wacce take kiba tana kuma kara girma da Wayau,gefe daya kuma Malika na ta Shiryen Shiryen Biki wanda Abun ya Hade mata gata wan mijinta ne,Gata kanwar amarya kuma kawa gareta,gata kuma ta wani bangaren tamkar Uwa take gareta Tunda komai na Shiryen Shiryen bikin Hajiya Binta ita ta sakarmawa Shiyasa koda yaushe cikin mgana Suke awaya don ganin yadda Abubuwan zasu tafi kan Tsari. *Am Srry For d late update,wlh haryanzu jikina sai Ahankali,and kuma kuyi hakuri da Typing errors bansamu lokacin Editing ba..* *MOMMYN LADINGO..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *31* """Shiryen Shiryen biki na cigaba da Wakana ta bangarori da Dama,kadama Uban gayyar yaji lbri yafi kowa Zumundin Aure Fiye da kowa shiyasa ya saki bakin aljihu ya sakarma Ummi kudi ta Aika Dubai akayo mata odar akwatuna da kuma kayan alfarma na gani na Fada,sai wanda ya gani akwati 10 cif aka Hadama Joda wanda kudin da"a ka narka kan kayan dake ciki ba kananan kudi bane.    Bikin an Shirya Sosai ta bangaren Amarya da kuma bangaren Ango,bikin na Saura Sati biyu Hajiya Binta ta kira Malika awaya tana Sanar da ita Dangin Mahaifin joda sun aikota mata kan basu yarda Joda ta zauna awajenta ayi Taron biki ba,suna bukatar Yarsu ta dawo wajensu da zama har zuwa Ranar Daurin Aurenta,Daga yadda Hajiya Binta ke mgana zaka gane bataji dadin Zencen na Dangin Mahaifin joda ba,ammh sai malika ta shiga bata baki tana Nuna mata babu ta kyale Joda ta tafi bakomai aciki sai su tattara su Bita chan malumfashin bayan andaura Aure aka dauko amarya bashi kenan ba,Kalaman Malika su suka kwantarma da Hajiya da hankali Sukayi mganar da zasuyi kafin su yanke kiran. Malika ita take Sanar da Saleem Abunda Dangin Joda sukace,bai damu ba yace hakan Shine Daidai Tunda gidan Wan mahaifinta Za"a Daura aure,daganan sai adauko amarya Zuwa Abuja basai ankara wahalan Zuwa Katsina ba,kafin ma Malika ta kira Ummi Ya marwan din yama su Ummi bayani kuma Suma sun gamsu,kuma Sunyi Na"am da hakan Tunda zai ma Fi sauki da ada sai ankoma ta katsina an Taho da Amarya...   Biki na Saura kwana goma Ummi ta Shirya kai kayan Auren Marwan,tare da kwalayen minti dasu Sweet sai goro da tabarmu harda buhun Shinkafa da Su Taliya da makori da sauransu da kudi 100k na amarya da kawayenta sai kayatattu  katinan da'aka bugo mussaman Domin Amarya,koda Ummi ta nemi malika datazo Ana gobe Abuja ta kwana Washegari suyi sakko Zuwa katsina in Hajiya Binta tagani dagachan sai Su Wuce Malumfashi,Aiko da Malika ta Sanar da Saleem murje ido yayi ya bala Toka yace wa..? Shi ba dan iska bane da zai barta tayi wannan Doguwar Tafiya ga Ayda jaririya kawai taje ta kwaso mata mura,kana kuma uwa uba Shi tatafi ta barshi da wane,Wlh kada ma tasaka rai bazata ba,Tun Tarihin zaman Saleem da Malika wannan ne karo na Farko daya hanata Abu taji Ranta yabaci wanda tayi kokarin Danne Fushinta ammh kuma ya gagara sai da ta bayyanashi,saboda takaichi sai da tayi kwallah,Ammh Saleem ko ajikinsa,da Ummi ta kirasa sai yayi mata karya da Malikan batajin dadi ne,kuma Ayda ma Tana mura baza ta samu Zuwa ba,harga Allah Ummi ta yarda shiyasa ta kira yan kumo suka taho Suka Dumguma zuwa kai kaya. Katsina Suka Fara Zuwa wajen Hajiya inda Taji dadin karan da'aka yi mata amtsayinta na Uwar diya,sai da suka ci abinci sukayi sallar azahar kana suka Damki hanyar Malumfashi,koda suka isa ba laifi sunga kara,dayake Ba Joda kadai za"a Aurar ba aiko yayanshi mata su uku joda ce cikon ta Hudunsu Tun Tarar da an kawo kayan Auren mutum biyu Aranar,suka Hada dana Joda cikon na ukun kenan,kuma Alhamdulillah Ciki duk Joda ce Tayi Zarrah,toh Pilot guda Wasa ne Dole akaga barin Naira,kunsan ance dama yanayin kayanku yanayin Tarbanku ne😂Toh su Ummi sunga karammawa sosai,sun kai suma kuma sun taho da Niki nikin Abun Arziki harda kudin Tukwaicinsu 40k aka basu Wanda Ummi ta nuna bazasu amsa ba ammh suka matsa musu suka karba ammh bayan Sun Nuna basu ji dadi ba.   ****************** Malika ko tagama Fushinta na kwana Biyu Dole Ta Hakura,Ammh tayi damarar Cewa Tun ana Saura Sati daya biki zata biyama Hajiya su Wuce Malumfashi biki,saboda Joda bata da Wata kawa kuma yar'uwa abokiyar Shawararta irinta so tana bukatarta akusa da ita,Da Farkon mganarta Saleem bai dauka da Gaske take ba,shiyasa bai dau Abun Serious ba ya Fita batunta don bayajin zai iya Rabin Malika tayi Nesa dashi Domin ya riga daya saba Rayuwa da ita,ko kwana daya Sukayi Batare da juna ba ya Fita jin jiki Malika ita tama Joda waya kan Ta samu Wacce zata mata Dilka da Halawa da kuma kunshi,in tazo zata biyamata,mganar mgungunar mata kuwa Maman Abba ta Hada ma Joda masu kyau da inganci dama ta iya Su gumba ne,su Tsimi ne,su garin aya,Hadin Bawon kankana,daidai Sauransu harda kaza da yan Shila mai mgani Malika ta Sanya akama joda,yan Uwanta ma na Dangin babanta basu barsu haka ba,suna basu Wata gumba da'a ka hadota daga sokkoto suna Damata kamar Fura da Madarar Yoghourt ko Madaran gari,Hajiya na gefe ta barma Malika komai Tunda itace Uwar Diya,shi kanshi Marwan din Da ita yake waya,shiyasa Saleem yace Ana nuna masa Wariyar Launin Fata,sai da yaga Ya marwan ya kira Malika,chan anjima kuma yaga Ummi ta kirata ayi ta kuskus shiko bamai kiranshi,daya gayama Ummi haka Dariya tayimai batace komai ba Itako Malika gwalo ta Dingamai Tana Dariya,shiko yana girgiza yake Fadin lallema Yarinyarnan zaki Shigo hannu ne..." **************** Biki na ragewa Saura Sati daya Tun Daren Jiya Malika ta Shirya kayanta tsab acikin akwatunanta guda biyu Wanda natane dana Ayda ta kuma Umarci Merry data Hada nata,don da ita Zata Tafi saboda kula da Ayda,shiko Saleem Sai da ya dawo da Daddare ne yaga kayan Malika tsab ashirye Abun ya bashi mamaki ganin har Washegari da Safe batamai mgana ba yasa shima ya Shareta yana so yaga iya gudun Ruwanta. Yana cikin dakinsa yana kokarin Daura Tek tie dinsa Malika ta Shigo hannunta Rike da Waya,gefen Gado ta Zauna tana Fadin"Mallam yau zamu tafi harma na kira Direba daga gida nace yazo ya kwashemu.."ido kawai ya sakamata yana Daura Tek Tie dinshi bai mata mgana ba Sai da ya gama yana kokarin Saka coat dinshi ne yace mata"Zuwa ina..?Kuma da izinin wa..? Ya fada Fuskarsa ba Fara'a. Jagale tayi tana kallonshi kafin tace"Bangane Zuwa ina ba Mallam..? Ka manta nayi maka mgana zan tafi katsina yau gobe mu Wuce malumfashi da Hajiya saboda Shiryen Shiryen biki..? Wayarsa yadaga yana Fadin"kuma sai nace miki toh na amince ko..? Ni azatona kawai kina mganarki ne.."Malika taji kwallar Sun Fara cikamata ido cikin Raunin murya tace"Mekaka nufi mallam..? Jakar brief case dinsa ya dauka yana Fadin"Kinfi sani ,so u better call d Driver ki sanar dashi kada yazo don inda kinga kinga bar gidan nan Toh ana gobe biki ne,bandama rashin Tunaniku na mata kitafi Tun yau nikuma sai kibarni na Zauna dawa,biki ba gobe ba ba kuma jibi Ba.."Yafada kanshi Tsaye yana nufar Wajen jerin Takalmansa bayason kallonta kada Hawayen datakeyi ya bashi Tsausauyi Malika dataji Abun yayimata Wani iri mikewa tayi tana Share kwallar data subomata tana Fadin"Ammh mallam kada kamin haka Don Allah,daga hajiya har Joda suna bukatata,kuma in kayi la'akari ina nataba Zuwa nayi kwanaki banda lokacin dana gama wankan Jego,don Allah kada ka hanani zuwa..."Bai kalleta ba ya Zura takalminsa baki Sawu ciki ya mike yana Fadin"Meyasa kikeso ki Fara Abunda ba halinki bane malika..? Na riga na gama mgana bafa zaki Tafi yau ba fakat bani son yawan gaddama.."Daga haka ya Fice adakin yana daga wayarsa dake Neman agaji Tun dazu. Wani kukan Takaichi ne ya kama Malika batasan sadda ta Fada bisa gado tana kuka ba,babu mai Rarrashinta Abunda yafi mata bakinciki meyasa Ranar datamai mgana bai ce bazata ba,sai da ya bari ta gama Shirya kayanta kuma ta saka rai atafiyar bayan ta kira Har Hajiya ta Sanar da ita yau tana Tafe,shine kuma zai hanata Zuwa kuka tayi sosai kafin ta dauki wayarta ta kira Hajiya muryanta a cunkushe tace kada Direba yazo bazata samu Zuwa ba yau.."Hajiya Binta yadda Taji muryan Malika tasan kila Saleem ne ya hanata sai bata damu ba,sai ma ta fara lallashin Malikan tana bata hakuri,Nuna mata tayi bakomai ammh kasan Ranta takaichin Abun yaki barinta. Ranar Wuni Tayi kwance,banda salla babu Abunda ke Tada ita ko girki bata Dora ba Ranar Tea kadai tasha merry kuma complex tace ta Hada tasha,ita kanta Ayda yau tayi Rigima saboda bata,bata nono yadda yakamata ba,Sai wajen bayan mangariba kana Saleem ya Shigo gidan da merry ya cikaro Afalo tana jijjiga Ayda dake kuka,Amsarta yayi yana tambayan ina mamanta take..? Merry tace tana daki yau kamar batajin dadi ne,Tunda yaji haka yasan Dalili koda ya Shiga dakin nata tana kwance,da alamun yau kazanta ne tataahi don ko wanka bata sake ba,Tunda da kayan daya Fita ya barta daso yazo ya sameta,cike da mamaki yayi tsaye kanta yana Fadin"Malika..."Yakirata cikin muryan Amo dagowa tayi tana kallonshi batayi mgana ba,mamaki tabashi mamaki ammh sai ya shanye mamaki ta hanyar kara Rumgume Ayda wacce ke Saman kafadanshi yana lallashinta yace"Meye haka..? Kina ji Ayda Na kuka ammh bazaki Fito ki amsheta ki bata nono ba,mekike nufi da yin hakan..? Mai da kanta tayi ta kife bisa Filo bata tanka mishi ba,ganin haka yasa Ranshi ya baci sai kawai ya kada kai ya Fice Zuwa Falo bai kara Tankata ba. Merry ya umarta ta kawomai madarar Ayda ta Sakamata Ruwan zafi ajikin Fidanta yana bata ta karba da Sauri tana ta Sha,daga gani tasha Yunwa,sai da koshi kana ta saki kan Fidan tana Wani maida Numfashi Tsausayinta yakamashi,Allah sarki yaro kenan,Rumgumeta yayi yana jin Bacin Rai game da Abunda Malika zata koya na wani banzan Hali,bata jima ba barci ya kwasheta nan ya mika merry ita shi kuma ya koma daki ya wanka ya Sauya kaya Zuwa jallabiya daganan ya Dauki mota ya Fice,sai da yayi sallar isha'i kana yaje yayo musu takeaway ya kawo musu,da kanshi yakaima Malika har daki bayan yabama merry nata Ya karbo Ayda Tunda yau matar gidan Tana Fushi dashi. Babu Abunda ya kara batamai Rai da lamarin Malika illah rashin cin abinci uwa uba kuma taki bama Ayda nono,ko da Daddare bai raba makwanci da ita ba,ammh ita ta juyamai baya kuma bayan ta maida kanta ta wajen kafafunshi,babu Abunda ya tsana irin mace ta juyamai baya,shiyasa shima ya Futa batunta Shi yayi ta bama Ayda madara cikin Dare har ya samu ta yi barci koda Safe Shi yayi mata wanka ya Shiryata Shima yayi wanka ya Shirya,ko kallon barayin da Malika take baiyi ba kuma Fuskarshi tana Daure babu alamun Fara'a itako Malika haushinta daya Don me yasan ya bazata ba,ammh bai sanar da ita ba sai bayan ta Shirya..? Koda zai Fice ko tak bai ce mata ba ya sakai ya Fice bayan ya mikama Merry Ayda yace ta kula da ita ko kuka take kada ta kaima Malika ta dama madaranta ta bata tasha ta goyata karban ta tayi tana amsa da toh Sir. Bayan Fitanshi ma Malika kuka tasha saboda ganin haryauma din bai ce mata komai,gashi joda ta kirata jiya tace mata bata samu tahowa ajiyan ba,ammh insha Allahu yau tana bisa hanya,ammh ta lura Mallam so yake Ta nunamai haryanzu malika malik din da bata Tafi ba,aiko sauranta kawai Ruwa ne ya daki babban Zakara Shiyasa ya ganta haka.. Har yatafi office da bacin Ran malika Shiyasa ko achan din Fuskarshi ba'a sake ba yana mamakin yaushe malika tadaina tsoronshi..? Yaushe kuma ta Rainashi haka..? ita kuwa tana kwance kiran Ummi ya Shigo wayarta bayan ta Dauka sun gaisa take tambayanta tana katsinan ne,Takaichi ne ya ciko malika ta sakama Ummi kuka tana Fadamata Abunda ya Faru,ran Ummi ya baci ta yanke kiran Ta kira Saleem yana dauka ta Rufeshi da Fada,Ta inda take Shiga batanan take Fita ba,daga karshe tace maza ya kira malika ya bata izinin tafiya bataso  iskanci,Saleem yaji zuciyarsa na Tafasa da zafi cikin bacin rai ya furta."Haba Ummi biki sai kace hauka Yaufa saura kwana 6 in ta tattara tatafi ni kuma na zauna dawa.."Ummi taji Haushi ta kunduma mai zagi da cewa"Ka zauna da Uwarka mana,koda kafin ka Auri malikan da ita kake kwana..,.? Kai bani son Dogon zence kayi Abunda nace kawai mallam in kuma bazaka iya bane ka Sanar dani.." Ranshi bace yace"Toh Ummi..."Daga haka ta yanke kiran tana Sababi ita kadai Abbi dake zaune gefe yana karanta Jarida ya dago yana Fadin"Aisha.."Aisha Shugaban matan Duniya,Kinga na haneki da Shiga lamarin yaran zamani kada Watarana kiji kunya atoh.."Tana kokarin Ficewa daga daki tacemai"Ba wani jin kunya Abbin Marwan,saleem din ne da ban Haushi wai kada ta barshi Shikadai,toh da dawa yake kwana..? Kaji wani iskanci.."Dariya Abbi kafin yace"Jiki da wata mgana nifa banga laifinshi ba,Ciwon Da Namiji ai na Da namiji ne so kona yi miki bayani bazaki gane ba.."Dariya Ummi tayi tana Fadin"Au hakane,toh shikenan Muma Ciwon ya mace na ya mace so ko nayi maka bayani bazaka gane ba.."Tafada tana tikar Dariya ta Fice daga bedroom din Abbi na tayata. Bai kirata ba kamar yadda Ummi ta umarcesa sai dai ya Turamata sako kamar haka _Kin kyauta Tunda ni ban isa nace Abu ba kiyi,shine kikeje kika Hadani da Ummi ko? bakomai Allah kiyaye hanya Bawan Allah bazai Wulakanta ba insha Allah.._ ya Rubuta mata ya Tura mata koda taga sakon duk kuma sai taji bata kyauta ba Nombarsa ta laluba ta kira,ammh har ta gama Ringing bai daga ba,ta sake kira ma Still bai daga ba,daga karshema latse kiran nata yayi ya kashe wayar gabadaya,Sai gashi Duk dokin Tafiyar ta Fita aranta taji da badon ta kira Hajiya tace ta turo mata Direba ba data hakura wlh,haka ta dinga gwada kiransa ammh wayarsa akashe har Direban yazo,dama aleady tun dazu ta soyamai miya da farar Shunkafa ta sakamai cikin fridge ta kuma soyamai Nama Shima ta ijiyemai kozai wahala kadan ne,Duk da tasan Mallam din nata akwai son jiki karshenta sai dai ya rinka Siyan abinci. Bata Wuce ba sai da ta Shiga gidan Maman Abba ta karbi sakonta na kayan matan data bata kudi ta Hadama Joda sukayi sallama bayan sun Rabu akan Ranar biki insha Allah zata biyo Baban Abba Tunda zashi Daurin Aure,Malika tayi murna sosai suka rabu akan sai tazo,Merry ita ke Rike da Ayda Wacce tasha wata hadaddiyar Bulawus mai kyau da tsari ga gashin kanta an tajeshi har merry ta daure mata shi da band dayake Ta biyo gashin uwar tata. Megadi shi ya taimakama Peter ya saka musu akwatunsu aboth din mota malika ta mai sallama kafin Su Fada mota su Fice daga gidan megadi na Daga musu hannu,sai da suka dau hanya kana Malika ta yanke shawarar Turama Saleem text sai ta Shiga wajen Rubuta sako acikin wayarta ta Rubutamai.    _*Am so srry mallam Bani da laifi wajen Sanar da Ummi komai,Banso mu Rabu ta haka ba buh Allah ya huci Zuciyarka we are in our way,In ka koma gida nayi maka miya,da abinci ka Duba cikin fridge,harda Nama soyayye,Sai mun hadu achan..I love u..*_ Tagama Rutamai ta Turamai suka Cigaba da Tafiya bata ga Reply dinsa ba sai da suka Shiga katsina kana taga ya Rubuto mata _Banso ban kuma gode ba,I swear zaki dawo ki tarar da Abunki.._ Daga haka bai kara komai ba,ita saima sakonshi yabata dariya ta Shareshi bata kara bi ta kanshi Ba. *Mommyn ladingo..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *32* ............"Hajiya Binta tayi matukar Murna da ganinsu sosai haka ta Shiga Dawainiya dasu Ayda ko Ram ta goyeta bisa bayanta tana jijjigata saboda yau tatashi da Rigima ne. Koda suka iso katsina Malika ta nemi Saleem awaya ammh bai Daga kiranta ba,sai tamai Uzuri ko yana Wani Abu ne,ammh Abunda ya bata mamaki har Washegari bata ga kiransa ba,kuma harda zasu Wuce malumfashi da Hajiya ,ta kirashi taji yayi hanging din kiranta A Number Busy kuma daya gama bai kirata ba,Abun sai ya bata mata rai Taga toh metamai Ammh ya Dau Wannan Fushin da ita,Tunda ga lokacin itama Tayi alqawarin Fita batunshi.     Duka gidan suka Tafi,sai aka bar Dose da Wata yar aiki da Hajiya ta Dauka sai sauran ma'aikatan Haraban gidan da megadi,Koda suka isa malumfashi a family House din Su Daddy Su ka yada zango wanda dama Tun Daddy na Raye ya gyarashi Sosai Adakin Hajiya Innaro suke sauka in sukazo wanda Shima yake gyare tsaf Duk da Wacce ta Haifi Hajiya Binta tana nan da Ranta acikin gidan. Malika bata Tafi gidan Baffan Joda ba sai da yamma Direba ya karisa da ita,koda tajema joda batanan tana makotansu inda ake mata Dilka da Halawa,sai da taje chan suka hadu,nan Suka Rumgume juna suna murna ganin juna cike da doki kafin su Zauna suna bayan sun gama gaisawa da Sauran yanmtan Wasu suna ta kallonta cike da mamakin anya wanna ce malika malik din da Suka sani..? Lalle Rayuwa juyi juyi na gaba yakoma baya Inda ada ne ko da kudi suka saka baza suga malika ido da ido ba balle har Su ganta akusa dasu haka. Malika nan ta tare Wajen Joda suna cigaba da Shiryen Shiryen,Ayda kuma tana Wajen Hajiya ita da Merry,sai inda ta Fara Rigima ne zata kawota ta bata nono Tunda babu Nisa da Family House din Su Daddy,An tsara komai cikin Tsari sai wanda ya gani bangaren ango ma ba karya domin Duka iyayan nasa sun baza Kudi sosai bayan Tarin gayyatan dasukayi Hardashi Marwan ya gayyaci abokan aikinsa Sosai. Saleema ma ta iso ana gobe Daurin Aure tazo ta tarar da gida cike da yan'uwa anata harkan arziki da Murnan Auren ya marwan,sai dare ne ta tambayan Ummi ashe Auren Zahra da Ya Saleem ya kare..? Nan Ummi ke Warwaremata Abunda ya Faru Tabe baki Saleema tayi tana Shaidama Ummi Nadira ce ke Sanar da ita Abunda Ke Faruwa tace Zahra ta zama Abun Tsausayi kuma tayi Nadama,Jinjina kai Ummi tayi kafin tace'Ko tayi Nadama bashi da amfani Saleema,dama ko addini ba'a son irin wannan Nadamar Saboda kana yinta ne,sanda Ruwa ya karema Dan gada,Kinga ko,ko kayita bata da Wani amfani agareka,shiyasa Amfison ka Tuba Tun kana da Sauran Damarka yanzu kuma babu Abunda mukayi iya Don Aure ya kare atsakaninsu.."Gyada kai Saleema tayi kafin tace"Wlh hakane Ummi,Allah ka tsarkakemana Zuciyarmu da imani.."Ummi ta amsa da"Ameen Ameen Saleema. Sai da yamma chan Sai ga Sadiq ya iso bai dade da isowa ba Sai ga Uban gayyan ya iso cikin motarsa 4 matic ya kara kiba da Fari kamar bashi ba,daka ganshi zaka Fahimci ya samu kwanciya hankali da Natsuwar Zuciya,shiko ya marwan sai chan dare ya dawo yana chan Tare da Wasu abokansa wadanda ya Saukesu a hotel,sai kalilan ne ya Saukesu agida suna tare dasu Saleem da Sadiq suna hira kamar ansan juna,Duk da Shi Saleem bamai yawan mgana bane,kuma yawancin abokan ya marwan din ba baki bane agaresa so Duk yasansu sosai. *************** Karfe 2:30 na Ranar Asabar Aka Daura Auren *MARWAN KABIR KUMO* Da amaryansa *JODA MUHAMUD MALUMFASHI* Wanda aka Daura shi kan Sadaki Dubu dari biyu lakadan ba ajalan ba,Daurin Auren daya samu Hallartan manyan baki daga kowani bangare kama daga barayin shi kanshi Uban gayyah,sai Saleem danashi Harta Sadiq Ba'a barshi abaya ba Uwa uba kuma Abbi da nashi Tawangan ga tawangan Sauran Daurin Aure guda uku Wanda suma ta kowani bangare sun Hallarcin Wannan Daurin Auren daya Tara Dimbim Jama'a. Maman Abba ta cika alqawari ta biyo Baban Abba sunzo Tare Wanda Sai dai Malika ta ganta kwatsam haka Suka Rumgume Juna Suna murnan ganin Juna,haka amarya Joda Wacce aka tsarama kwalliya ta Nuna tsara tana Sanye da Wani leshi mai kalan Blue black da Ratsin kwalliyar pick,sai mayafinta ma pick da jakarta da takalmin kafanta,sosai taji dadin Zuwan maman Abba,haka ta Rumgumeta tana mata maraba da Zuwa,Ita kuma Tana mata Tsiyan Amarya tasha kamshi .   Ana gama Daura Aure da Awa daya bayan sungama sallaman bakin da zasu Tafi sai kuma suka koma Shirin komawa Abuja da amarya,wacce aka Dauketa daga nan gidan data ke party Zuwa Family House din Su Daddy Inda Hajiya ke taronta ita da Danginta domin suyi Bankwana,lokacin ita kuma Malika suna Tare da Maman Abba ta rakota kofar gida Baban Abba yace ta Fito su Wuce,shine ta roki alfarman ya dan mata lamani taje tama Hajiya Allah Sanya Alheri Tunda babu Nisa,dakyar ya yarda Ammh da Sharadin bazata Dade ba. Malika na Sanye da Leshi ne mai maroun colour wanda keda kwalliyan Ja ajikinsa,Riga da Sikat wanda ya Fito da ita Sosai itama an mata kwalliyan Duk da ba cika mata akayi ba,ammh kam kallo daya zaka mata ka fahimci dama chan tana da Sirrin kyanta,mayafin data yane kanta Dashi Ja ne,mai wasu Ratsin Duwatsu masu daukan ido,hakama takalmin kafanta baki ne mai daurin igoyoyin ja ajikinsa kunsa mutuniyar akwai son Takalma masu Tsini da Tudu. Ayda ce ahannunta Wacce itama taji adonta cikin Riga da wando,Rigar Pick ce,wando ko na Jeans ne baki sai wani takalminta mai kyau da Tsari pick colour kanta ko yasha kitso wanda aka sanya band din kanana aka kama mata Daki daki,Sun Fito da Maman Abba zasu koma Family House din su Hajiya,duk akwai maza sosai akofar gidan da kuma Tarin hadaddun motoci,.   Saleem ko da suke jingine jikin motarshi Shida Sadiq da wani abokin ya marwan mai Suna Hamza,sai Baban Abba,dukkansu sunci Dayan Shaddodi Farare dinki Muhammed ne wanda ya dace dasu Samarin zamani,Lokacin da su malika Suka Fito hankalinsa na bisa waya bai gansu ba,Sai da Sadiq ya tabosa kana ya Dago ya Sauke ganinshi kan malika tana tafe sabe da Ayda suna hira da Maman Abba tana sakin mata kayatattacen mirmishin din,Wani yam Saleem yaji lokaci daya yaji Ranshi ya baci ballema Daya ga da Sadiq din har dabHamza sun kura mata ido,yana ji Sadiq na gayama Hamza mai jan gyalen nan matar Acp ne. Tuni Ran maza ya baci,idanuwansa har sun kada saboda kishi wayarsa ya Cigaba da dannawa kamar babu Abunda ya Dameshi Sako ya Turama malika kamar haka _Ki tsaya a inda kike ganin zuwa,ban Amince ki kara ko taku daya ba._ Tana jin Shigowar sako Dama wayar na hannunta tana Danna Sreen din Sunanshi yana Wayo ta saman Wayanta Dauke da Sunan data Sanya mai * ABBU AYDA* Mirmiahi tayi kafin ta Shiga sakon da ya Rubuta ne ya Daure mata kai ta Dakata da Tafiya tana waige waige ganin Haka yasa maman Abba tsayawa tana Fadin"Matar Acp lafiya kuwa...? Kowani kike nema..? Miyau ta Hadiye kafin tace"Kinga mallam ne yamin Sako yanzu yace na jirashi gashinan Zuwa,kuma inata waigo banga ta inda zai bullo ba.."Tafada tana Raba ido,mirmishi Maman Abba tayi kafin tace"Baki lura dashi ba gashi ta bayanmu yana Tahowa aie..."Da hanzari Malika ta juya sai ko ta hango Saleem yana takowa wajensu cikin takunsa na isa yadda taga yanayin Fuskarshine Sai da Firgita,cikin jin kai ya kariso garesu maman Abba na gaisheshi ya amsa cikin sakin Fuska kafin ta danyi gaba,Malika ta kalleshi taga ya Hade rai duk sai ta Daburce cikin sanyinta tace"Mallam ina yini.." Bai amsa ba ya mika hannu yana Fadin"Bani ita Kirjin biki..."Yafada kai tsaye yana kallonta batayi gardama ba Tamikamai Ayda ya karbeta itako tana ta wangalemai baki dama Tunkafin ya karbeta bai kalli malika ba ya Juya yana Fadin"ki koma ciki malama ban amince kije ko'ina ba,yanzu zamu Wuce Abuja in kuma baki gama bikin bane,in ngama ganin Ayda zan aiko miki da ita ciki.."Daga haka ya juya ya Fara Tafiya,Kunya da Haushi suka kama Malika tayi jagale tana kallon Bayan Saleem kafin ta saki ajiyar Zuciya ta karisa kusa da maman Abba tana Sanar da ita Yadda suka yi da Saleem,dariya tayi mata tana Fadin"Kishi ne ya taso karki damu bari naje kila in yagama dama ya biya dani ko Sharp sharp ne mu gaisa.."Jin haka yasa sukayi sallama dama Tun aciki malika ta bata kayan biki musabaha sukayi kafin su Rabu malika takoma cikin gida itakuma maman Abba ta Nufi Baban Abba wanda har ya Shiga mota Shida Abba ita kawai suke jira. Malika ko data Shiga cikin Abun sai yaki barin Ranta sai da tayi kuka aboye,Kafin ta dauro alwala bayan ta Wanke Fuskarta tana cikin sallah ne kawayen amarya suKa Dinga zuwa daukansu suna Fadin gashi chan za"a tafi bata damu ba,don ko da ta idar sallar bata Fita zaman ta tayi tana mamakin mallam,shifa yake koyar da ita hakuri ammh yau gashi laifi kadan ya Riketa dashi yakasa yimata Afuwa. Tanan zaune sai ga kiranshi kamar bazata Dauka ba sai dai ta daga kiran cikin Gadara yace"Kina ina..? Ranta acunkushe tace"Ina cikin gida.."Kifito ki karbi Ayda mu zamu Wuce ne.."Daga haka ya yanke kiran,Wayar tabi da kallo kafin tatashi ta Tafi,Abunda ya kara mata mamaki mikomata Ayda Yayi ya juya zai Shiga mota sai itacene tace"Mallam ni wata mota zan Shiga..? A karkarce ya kalleta kafin yace"Zuwa ina..? Kwallar har sun Fara cikamata ido tana kallonshi tace"Zuwa Abuja.."Tana Fada cikin Sanyinta,Ganin yadda tayi ne yasa ya sauke ajiyar Zuciya yana kallonta akarkace kafin yace"Au yau zaki koma kenan..? Ni zatona sai kin sake Wani satin kinga ko sallaman Jama'a kya taya Hajiya.."Jin Abunda yace ne yasa taji Zuciyarta ta tsinke batamai mgana ba ta juya,ganin haka yasa ya Sha gabanta yana Fadin"Ki Shiryo kayanki mutafi don Tun dazu su ya marwan da tawagar amarya Suka mika.." Bata kalleshi ba ta mikamai Ayda ita kuma takoma cikin ta dauko karamar jakarta bayan tama matar gidan Sallama Tunda anan suka zauna Tsawon kwana uku,Koda ta Fito Shida Sadiq ta gani yanzu,ba don Sauran kayanta na gidan Su Daddy ba,da Saleem baida niyyar biyawa,Allah dai ya Dorata akanta ta Biyama tama Hajiya sallama suka kwashi kayansu ita da merry,shi kuma ya bude musu booth suka saka kafin su Fada mota su dau hanyar Abuja. Ko amotar kanzil bai cemata ba,itama bata tankashi ba,shida Sadiq suke ta hiransu sai wani lokacin ne Sadiq ke sakota ciki  itako sai da ta murmusa,shiko Saleem da Sadiq ya sako malika zai dauke baki ya hade rai,Tun Sadiq bai Fahimta Ba har yagane ma'auranta sun Samu mtsala,baiyi mgana ba kawai yayi musu Fatan Allah Daidaitasu domin yasan koyayima Saleem mgana ba Kulashi zai yi ba. ******************** Su ya marwan sun isa ba Dadewa sai ga su malika,Ummi ta Rumgumeta tana murna Abun mamaki Saleema tazo tana gaishe da malika ta kuma yi Saurin karban Ayda tana mata Wasa,sai ga Saleema ta dauki akwatunan Malika tace dakinta zata sauka,Ummi na mata tsiyan yau kuma Anty malika akayi Uwar daki da ita,tace eh yau Ummi ba bakuwar ki bace tawace. Dakinta ta kaita ta Hadamata Ruwan wanka da kanta Ta Shiga tayi kafin tazo ta rama sallar mangariban data samesu ahanya,tana zaune kan Dardumar aka kira Issha'i ta mike ta gabatar kafin ta Fice Zuwa Shashen baki inda aka Sauke su Joda,ko da joda da kawayenta da yan'uwanta suka ganta sai suka Fara mamakin wace mota ta Shiga joda ce ke dariya tana Fadin"Lalle masu abu da abunsu mallam ne ya taso Abunshi.."Dariya malika tayi tana ma Jodan dakuwa,ta iskesu ankawo musu abinci kala kala da Abunsa suna yaba kirkin Dangin Marwan da mahaifiyarshi,Dariya kawai malika tayi tana kara gayamusu haka suke kowa nasu ne musamman Ummi da Abbi. . Batabaro dakin ba sai wajen goma na Dare Saboda ta karajin barci ga gajiyan zirga zirgan biki inda Allah ya taimaketa ma Ayda na Wajen Saleema kilama tayi barci,Falon babu kowa sa yan kumo suna hira,gaishesu tayi suka amsa cikin sakin Fuska suna tambayan Ayda tace tana Wajen saleema,daki ta Wuce koda ta Shiga ba kowa Saleema bata ciki,kila tana sama wajen Ummi,yadda barci yaci idonta ne yasa bata tsaya komai ba Ta kwanta tana jan blanket ta Rufe kafafunta dashi,cikinta kuma acike yake shiyasa bata nemi abinci,ba ko minti goma batayi barci ya kwasheta Saboda gajiya ko addu'an barci batayi ba. Saleema ko tana Falon Abba,suna hira dukkansu iyalan wadanda sukan Dade basu hadu ba,ya marwan da ya saleem da ummi da Abbi da Sadiq sai Wajen 12 kana suka sauko bayan Ummi ta koresu tace zasu kwanta suma barci suke,Koda Saleema ta Shigo dakin dauke da Ayda Wacce itama ta dade dayin barci ahannun Abbi,ganin Malika na barci sai bata tasheta ba,ta kwantar da Ayda gefe itama ta Shirya cikin kayan barcinta kafin ta hayo gadon bayan Ta Rufe musu kofa kuma ta rage Wutan Dakin Kusa da Ayda ta kwanta tana kamkameta kamar wani zai Rabasu,dama ko banza Saleema irin Abbi suna da Son yara kanana. *MOMYN LADINGO.* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *33* ..................Malika Saboda gajiya dakyar ta iya tashi sallar asuba koda ta idar idonta na Rufewa ta koma bisa gado,wani barci mai Nauyi ya sake Daukanta bata tashi ba sai pass 10 lokacin data tashi har Saleema tama Ayda wanka ta goyata,baki ma Tuni sun yi wanka sun karya Wasunsu Duk Sunyi Shirin Tafiya expecillay kawayen Joda da suke Zaria da kaduna Wadanda sukayi mkranta tare. Yan kumo ma koda tatashi Tuni motarsu ta mika,lalle tasha barci itama wankan tayi ta Shirya cikin Wata Atamfa blue mai kwalliyan pourple ajikinta,Ta daura dankwalinta irin Daurin Zahra buhara,Sai da ta karya kana ta Saka babban Mayafinta ta yane kanta dashi kafin ta Fita tana gaishe da Ummi da Ya marwan Data ga suna mgana,Saleem na Wajen Shida Sadiq gaishesu Tayi Sadiq ne kadai ne ya amsa cikin sakin Fuska,shiko Mallam Fuskarsa ba Annuri ya amsa mata da lafiya lau,daganan ya Dauke kai Duk da yana Satan kallonta ta Gefen ido domin ba karya ta mai kyau sosai a ido kamar yatashi yaje ya Rumgumeta ya fadamata irin missing dinta dayayi ammh bazai iya ba,Tunda ita datayi laifi ta gagara bashi hakuri shiko bazai bata, sai sun koma gida suciga ba daga inda suka Tsaya.    Daganan Shashen Da'a Sauki su Joda Ta nufa taje suka gaiggaisa chan tama tarar da Saleema,sai lokacin taga Ayda wacce ke barcinta lum abayan Saleema,ko da tashiga Duk suna ta haraman Tafiya ne,nan sukace tama ya marwan mgana Kawayen Amarya zasu Wuce,awayar Joda ta kirashi ta Sanarshi yace Su Fito koda suka Fito sukama Ummi sallama ta basu 20k tace su raba kafin Marwan yasa Direba ya kwashesu Zuwa tasha su hau mota su hudu Ne Shima 20k din ya basu yace Suyi na mota suka karba suna Godiya     Koda Azahar tayi gabadaya yan kawo amarya sungama Shirinsu suka taso keyar Amarya Joda Zuwa Falon Ummi suka Damka amanarta gareta tare da yan Nasihu sai manya Robobi guda biyar,Daya na cincin,daya na Dubulan,daya na Alkaki,daya na hikima,daya na Nakiya,sai Buhun shinkafa Biyu dana Tuwo daya sai kwalaye suma Sunfi Ashirin gasunan burjit,ba laifi dangin Uban Joda sun mata kayan gara Sosai kusan katsinawan Dikko akwai kaya da Babban Harka.😂 Ummi tayi ta Fadan meyasa suka Wahalar da kansu,sukuma sukace ai bakomai an zama daya basu zauna ba Suka bar Joda nan suma Direba ya kwashesu Shi zai maidasu Malumfashi,bayan Ummi ta cikasu da kudi da Turaman zannuwa aka Rabu cikin Mutumci da karammawa. Sai Da daddare kana Abbi ya tarasu gabadayansu yayi musu Nasiha da Fada mai Ratsa jiki,wanda kowa Nasihan Abbi ya Shigeshi musamman Wajen da Abbi ke Nusar dasu hakuri da Mazajensu da kuma girmama Aure wanda Abu ne mai matukar amfani kana ya horesu da yaki da Shedan azamantakewarsu komai ya Shiga tsakaninsu na bacin rai kada su kullaci Juna Su tsaya su Saurari uzurin Junnsu su kuma ba junansu Hakuri wanda indai Sukayi haka Har Abada bamai jin kansu,kana daga karshe ya Horesu da su zama Tsintsiya daya madaurinta daya Domin Dukkansu yanzu sun zama Ahali Guda Daya,koda akabama Ummi damar mgana bata ce komai ba Domin tace Abbi ya gama mgana Albarka tayi ta saka musu,Hajiya ma ta tofa albarkacin bakinta daga karshe ta karke musu da Tsiya da mutunin nata Saleem,wanda yake Wani cin mgani,kamar wanda akama Dole.    Tare Sukayi Dinner dukkansu Harda amarya da ango wanda ya zaku abashi dama ya kebe da amaryansa,Aiko suna gama cin abincin Abbi da Ummi suka Haura sama,shima yaja matarsa suka Fada dakinsa suka yi lum dasu,Sadiq ko afalo suka yada zango Shida Saleema Suna Hira,Saleem ko Dakinsa ya Shigo yana Dauke da Ayda ganin haka yasa Malika komawa dakin Saleema ta kwanta tana Tunanin mafita,Aranta taji komai ya sauka Duk Fushinta itama ta Saukeshi Takuma kudiri niyyar bama mallam Hakuri da Zarar sun koma gida   Barci yafara kwasanta taji Bude kofa da Shigor mutum kamshin Turarensa kadai ya tabbatarmata da Shine,sai ta kara lafewa jikin katifa kamar mai barci gabanta yazo ya Tsaya yana Dauke da Ayda Wacce take ta Sharar barcinta cikin Aminci,Dukawa yayi ya Kwantar da ita gefen Malika yana yafa mata blanket din da malika ta Rufe rabin jikinta dashi... Hannayensa Duka ya Tura acikin aljihun Wandon barcinsa na pjm,Yana kallon Fuskar malika cike da so da kauna Hade da Wata kewa,Rankwafa yayi yana kallon karamin bakinta da kirjinta wanda ya kara cika,Kamar zai kai hannu ya Shafa mata Fuska sai kuma ya Fasa,yana tsuramata ido saboda yaga kamar tana motsi kenan ba barci take ba,Asirinta ne ya Tonu da mirmishi ya Subucemata bata Shirya ba,Agaggauce ya dago yana Kara Tamke Fuska yayi Saurin Juyawa zai Tafi ta damko hannushi da Hanzari,bai waigo ba yace cikin muryan Dakewa "Meye haka kuma..? plz leave my Hand.."Yafada yana jin Wani iri kawai yadda ta kamkame hannun nashi,Jin Haka yasa sai ta kara narkewa cike da Shagwaba take Fadin"Haba mallam..,Ni..Ni ko nice fa Yar Amanarka kadaina sona ne yanzu..? Muryanta ta narkar dashi ya dago yana kallonta yadda take wani lumshe ido Baki ya tabe kafin yace"Keba Amanata bace,don da kin dauki kanki ahaka da bazan hanaki Abu ba,ki mtsama sai da kikayi,Mganar ko na Daina Sonki ne Eh na daina Sonki ko da mgana ne.."Yafada yana Tara gashin Giransa waje Daya. Mirmishi ta sakarmai tana kokarin mikewa kenan Sai ga Saleema ta Shigo,ganin hannunsu sarke cikin na juna yasa ta koma da baya tana Fadin"Oh!Srry..."Tafada tana kunshe dariyanta ganin yadda ya Saleem yake maka mata Harara,Ganin haka yasa malika ta sakeshi tana kallonshi bai kara bi ta kanta ba ya Fice daga dakin Duka hannuwansa suna cikin Aljihun wandon barcinsa kamar wani basarake.    Girgiza kai tayi ta mike daga Kan gadon Tiolet ta Shiga ta Dauro alwala tazo ta yi Shafa'i da Wuturi kafin tayi Shirin barci ta kwanta tana Tunanin mallam dinta wanda tayi Kudiri Niyyar sai sun koma Zamfara zata Shiga Fagen lallashi Ta lura bazai sauko da Wuri ba,har tayi barci Saleema bata Shigo ba itako Saleema dakin Hajiya taje tayi kwanciyarta Azatonta ya Saleem zai kwana wajen Malika ne,Tunda ya Sadiq na dakinshi. ********* Washegari Tun 7 Saleem yakai Sadiq airport inda ya Shiga jirgi yakoma wajen aikinsa,itama Saleema koda karfe 9 tayi ita da Direba sunyi nisa ahanyar komawa kano,dama Weekend ne tazo,suna da aiki sosai a asibiti ,Shima Saleem wajen 12 din Rana ya Fito cikin Shirn sa na Tafiya yacema Ummi zai Wuce da Ummi tamai mganar ba tare zasu Tafi da malika ba,sai ya tamke Fuska yace gobe Direba yazo da ita,shi yanzu sai ya bi Wani waje ba zamfara zashi kai Tsaye ba,kanzil Ummi batace mai ammh Tana Lura da Saleem da malika wannan Zuwan ba wata jituwa atsakaninsu,bata yi Shisshigi ba balle tazo taji kunya Fatan isa lafiya tamai Domin tasan ko tace ya tsaya Su Tafi tare da Malika sai ya bata mata rai Don Shigen Taurin kai gareshi. Malika bata da masaniya sai dai Fitowa tayi ta iske Saleem ya Tafi,tana duba wayarta kuma taga ya Turo mata sakon _Ummi tace mu Taho tare nayi mata karyan Ba Zamfara zani Direct ba,Ban yi ra'ayin Taho dake bane,so wanda ya kawoki sai kimai mgana ya maidoki.._ Sakon nashima Dariya ya bata sai Da ta kyakyata ita kadai tana kaunar Halin Mallam Shifa akomai na *MALIKA MALIK.."!* _Sai na rama ne_ Bata damu ba illa itama ta Hau Shirin tahowa don batason daga gobe takara kwana kada ta kara wani laifin. Joda ko da ya marwan basu Fito ba sai bayan Azahar Amare kenan Akwana a Hantse inji Hajiya Babba,Dukkansu sai Shekin amarci suke suna walwali kamar Zara da Wata,daga gani Ya marwan baiyi Wasa ba,don Joda idonta ya tona mata asiri saboda yadda ya kode saboda kuka,koda suka kebe da malika adakin Saleema kuka ta sakama ta Ita kuma tana mata Dariya,aranta tana Fadin!Uhmm joda aike bakiji komai Tunda har kika iya Tafiya da kanki,nice Wacce tafi kowa jin maza Tunda harda su Dinki da jinyar Sati biyu,ammh afili sai ta Shiga lallashinta da bata wasu Shawarwari Wadanda zasu amafeta,tare suka Wuni Ranar hatta Dinner ma tare suka taya Ummi Shiryaawa sunayi suna Hiransu Cike da Kaunar juna da Soyayyar,wanda kaunar Ummi ya cika ransu ayayinda itama kaunar Surukan nata ya ki Boyewa acikin Ranta tayi ta godiya ga Allah daya Hada Zaratan ya'yanta da mataye na gari tare da Fatan zaman lafiya a tsakaninsu har Abada... ************ Malika Tun Safe tagama Shirinta ita da Ayda da Merry,Direba ya kwashesu sai Zamfara,sukansu su Ummi da Abbi Sunji kewar Tafiyar malika mussaman ma Ayda Wacce ta Shiga Ran kowa.   Da Wuri suka isa Wajen Azahar Direba Ruwa kawai yasha ya juya ita kuma suka zage suka gyara gidan Abunda ya bata mamaki wlh Saleem bai taba abinci datamai ba,harda miyan data hadamai,dama ya Fada,ta zata Wasa ne ashe da gaske yake miyar dai batai komai ba,da soyayyen Nama,wanda saboda ya Soyu sosai,sai ta zubar da Shinkafa kawai ta gyara kicin din kafin ta Dora girki Duk da Uban gayyah baison da Dawowarta ba,so take yau ta wanke laifinta kaf.    Sai Bayan la"asar ta Dora girkin Megadi tabama kudi yayi mata cefanan miyar ganye Ta yimai Tuwon Semo,don ta san mutumin nata yana Son Tuwo kowani iri ne yana Son Shi da miyar ganye,bata gama ba sai gabda mangariba,lokacin ta Mulmulashi a leda ta zubasu cikin kololinta masu kyau da tsari,Ta gyara kichen din kafin ta Fito tA karbi Ayda ita kuma saka merry tace takara gyara mata Falon ta sakamata Socket din Turaren Wuta. Wanka ta Shiga tayi ,tayima Ayda suka chakare,bayan tayi sallar Mangariba,Wani material less dinta ta saka Doguwar riga wacce ta Fito da Tsarinta tsab dayake Rigar Ashape ce,ta ci daurinta wanda ya zubomata da gashinta bayan ta saka band ta matseshi ta baya,Ayda taci wata Doguwar rigar bulawus mai bulewa itama harda Jan baki Malika ta saka mata domin Taran Abbanta...   Bayan issha'i motar Saleem ta sawo kai gidan Bayan ya Zuba hon megadi ya wangalemai get ya Sulala ciki,Malika na jin tsayuwar motarshi yasa ta Fada daki da Sauri ta Fara mata kanta Feshin Turare,sai da tabbata da kowani lungu Ya samu mazaunin kamshi kafin ta Fito Falo tana takun isa,Shiko Tunda ya doso kofar Shigowa Falon,yaji wani kamshi ya dakeshi Lumshe ido yayi yana Shafa kanshi afili ya Furta"Lalle na yarda mata ne Ni'imar cikin gida.."Yake Fada yana Mirmishi Shi kadai kafin ya saka kanshi cikin Falon da sallama hannunsa na kada key din motarsa sai wayarsa dake Rike A hannunsa.    Da Malika ya ci karo Wacce take kasheshi da murmishinta Tundaga Nesa,wani sanyi ya ratsashi tsaye yayi yana kallonta ita kuma tana wani Taku Zuwa gareshi kamar Wata Wahainiya tana Zuwa ta Fada jikinsa daga ita har Ayda tana wani Narkemai ganin Sunyi baya ne kamar zasu Fada yasaka Duka hannunsa ya tarbesu dashi ya Rumgumesu tsam ya matsesu yana sakin Wasu tawagayen ajiyar Zuciya,Ayda ko tana ta taba Sajensa tana gwarancinsu na yara,tana wangale baki bata gane iyayen nata Sun Shiga wani yanayi ba.." Kiss ta sakarmai awuya tana Fadin"Nayi kewar malamin mijina.."Tafada tana,Kara lafemai kamar wata mage,Ajiyar Zuciya ya saki kafin yace"Nima nayi kewar marajin matata Sosai,Malika kece Farincikina.."Yafada yana Sumbatar Tsakiyar kanta,Shuru tayi kafin tace"Baka na Fushi dani ba,kai akomai na Malika sai ka rama ko..? Yar Dariya yayi kafin ya Rabata da jikinsa yana kara Rike Ayda yace"Ashe kingane,Ammh Kadan nake Ramawa saboda in na Rama da yawa yana Zurmawa dani.."Yafada yana Dagamata gira,Hannunsa ta riko tana Dariya tana Fadin"Tuba malika take,Mallam yayi mata Afuwa bazata kara nuna damuwa ko Bacin rai game da Hukuncin ka ba.." Suna tafiya Zuwa hanyar dakinsa yace"Gud matar Aljannah,Allah miki albarka ammh na dade da Hucewa kawai Ramawa nima nakeyi.."Yafada suna Shiga dakinsa kan gado ya kwantar da Ayda kafin ya kamo Malika ya Rumgemu yana Faman Shinshinar Wuyanta,hannayensa kuma yana karakaina ajikinta,itama matseshi tayi tana Sauke ajiyar Zuciya kafin ya lalubi bakinta yana bata wani irin kiss mai tsaya a zuciyar wanda aka yimawa.    Da malika taga Saleem ya Rikice mata,Dakyar ta yakice jikinta ta Dauki Ayda ta mikama Merry ta dawo Mallam ya Dasa sabon karatunsa,domin yayi kewar Dalibarsa tasa sosai,Susuce mata yayi yana zayyanamata yadda yayi kewarta itama zagewa tayi tana mai salo salo mai Tafiya da Zuciyar masoyi,sai da suka dawo natsuwarsu kafin ya Kwasheta Zuwa Tiolet ko awajen wankam ma Rabi da rabi Duk Romance ne da tsotse tsotse,Shikanshi wanka dakyar sukayi bayan kowanne yayi wankan Tsarki,Suka Fito suka Shafama juna mai cike da Soyayyah ko abinci ma Ranar cikin Bedroom ta kawomai nan suka ci,tana kan cinyarsa tana cinyar dashi,shima yana cinyar da ita cike da Soyayyah da kauna,Ranar dai an gantale suka kare😂😂,don kololin kadai ta tattara Zuwa kichen,kafin ta Dawo suka Cigaba daga inda suka tsaya Ranar dai Ko Ayda Wajen merry ta kwana Tunda taga iyayen nata Tunda suka Shige daki ko lekowa basuyi ba,Shiyasa itama tayima Ayda Shirin barci suka kwanta. Ko Washegari basu Fito da Wuri Ba,sai da Merry ta buga musu kofa Ayda na Rigima kana malika tazo ta amsheta,Ranar Saleem ko aiki baije ba yana Nanike da Matarsa da yarsa Abun Alfaharinsa wanda ko Kuda bayaso ya tabasu saboda yadda yake Kafa kafa dasu,itama malika haka take,Duk Abunda tasan Saleem bayaso tana Gudunshi,shiyasa yanzu karatun nasu ya Dau Nisa,don Malamin nata ya Rike mata wuta,Rabi karatu ne Rabi kuma Karatun Samun lada ne,Wanda dukkansu yanzu sun zama cimgam din juna ko gajiya basuyi,kowanne baya gajiya da Rabar jikin Dan'uwanshi. _Ina kai kyakyawan gaisuwata Zuwa gareki KAWA😘💕 *MALAMA JUWAIRIYYAH,* Kawata abokiyar Cin mushena,alherin Allah yakai miki Aduk inada kike,Allah kuma yabada Sa"an mkranta,Ammh wannan Sakon gaisuwa ne da kuma cigiya don kwana2 najiki Shuru ne,Allah yasa Lafiya Ameen_ *Mommyn ladingo..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *34* ..................."""Rayuwar Farinciki tare da Wata Soyayyah mai tsayawa azuciyar masoya Shi Saleem da Malika Suke gudanarwa gwanin ban Sha'awa ga Wanda ya gani,Yadda take mai ladabi da biyayyah yafi komai burgeshi da ita,uwa uba kuma komai zata gudanar sai da Shawaranshi da kuma izininshi. Malika tana da tarin Dukiya wanda batasan iyakarta ba, akallah bankunanta sunfi guda 5 kuma kowanne banki Duk wata riban kudi na miliyoyi suna Shigo mata harma ta rasa wani Tunani zatayi domin Taimakon al'ummah Dashi Domin dai ita bata da muradin kudi ayanzu haka Kudinta shine mijinta da Yarta,yana mata komai na bukatan Rayuwa da cigaba baya duba tana Dashi komai dayasan hakkinshine yana kokarin kare mata shi Har gobe Kudin da malika ta mallaka bai taba Tsole mishi ido ba,Yana kokarin Dorata ahanyar mai kyau tare da kyakyawan Shawara Domin Rabauta daga Duniya har Zuwa gobe kiyama.. Mganar Filayen datace a bincikamata a malumfashi an samu har Saleem yaje ya gani an kuma yi ciniki da dillallai an biya kudin manyan Filayen Guda biyu wanda aka bashi Duka takardun Filayen mai dauke da Sunanye malika,batayi wasa ba tabama Saleem Duka dama,shi kuma sai ya Umarceta data bama kawun nan Daddy dake nan Malumfashi kwangila kula da ginin makrantan da masallacin Saboda sune ke gari,shi kuma yana Nesa,ammh yamata alqawari lokaci bayan lokaci zai Dunga Zuwa yana Duba aikin. Haka ko akayi ta Tura musu Kudin da zasu isa Duka aikin nan da anan aka bama ma'aikatan gini kwangila,suka Fara gininsu cikin Nasara Abunka da Kudi kafin kace kwabo gini yayi Nisa kuma Alhamdulillah Da Saleem zai je Duba aikin Tare da Malika Sukaje,taga komai da idonta ta kuma yaba,awajen ma Sai da tayi kwallah Saboda Tunawa da Daddyta datayi ammh tana mai addu'an Allah jikansa da Rahma. Tabiya Family house dinsu sun gaisa Duk da bata zauna ba,tama iske Hajiya ta koma katsina Satin daya gabata so basu hadu ba,Haka Dangin Daddy suka taru suna sakama malika albarka,itakuma sai tace su godema mijinta Domin Shine Silan zamowarta Duk Abunda ta zama ayanzu,Domin da babu Shi acikin Rayuwarta da yanzu batasan awani Hali rayuwarta Zata Shiga Ba. ********** Joda da marwan Sati biyu sukayi gidansu Ummi suka tatattara su ka koma lagos wajen aikin mijinta,wanda kafin su tafi sai da ya kaita malumfashi tayi sallama da yan'uwa da abokan arzuka kafin yakaita Zamfara tayi musu kwana daya ya kaita katsina wajen Hajiya nan ta kwana daya,tana Dawowa suka tattara suka tafi suka bar su Ummi Cike da kewa. ************ *INA LABARIN ZAHRA* Zahra dai tana cikin gararin Rayuwa Domin daga Abba har momi sun Fita batunta bamai Kulata balle ya Shiga Sha'aninta har gwarama Nadira takan xauna ta lallasheta in taga tana kuka,ko ita din ma ba kamar da ba,kowa laifinta yake gani. Zahra kishinta yakaita ga aikata Abunda yazo yana damunta,gashi tana Bala'in son Saleem ammh lokaci daya Zuciyarta da Sharrin Shedan suka Taimaka wajen Nesanta ta da Abunda tafi kauna Duk Duniya,bata Fitowa kullum cikin daki tana kwance tana kuka,shiyasa kafin tagama idda duk ta lalace ta kwarzane kamar ba Zahra ba mai iyayi da Rawan kai yanzu Duk bashi,sai ki ganta ta zauna tayi Shuru tana Sharan Hawaye kamar ba ita ba. Ganin haka yasa sai momi ta Fara jawota ajiki ganin tana neman kashe kanta da Tunani,ammh Duk da haka zahra bata dawo da karkashinta na baya ba,Duk da ko Daga momin har Abba yanzu Sun Yafeta sun koma mata addu"an Allah ya Cire mata wannan mugun kishin kuma ya bata Wani mijin na gari. Satin daya wuce suka Sha Bikin ya Nadir inda ya Auri Wata Scientics Aisha bala,Itama anan Asibitin Aminu kano,anan Suka Hadu suka Fara Soyayyah har ta kaisu ga Aure.Auren da akasha Shagali sosai Duk da Zahra ta dan Warware ammh ba kamar da chan ba,suna zaune awajen Asibtin Aminu kanon nan ya Nadir ke da gidanshi mai kyau da tsari. Awajen bikin ne Nadira ta Hadu da Wani DR HAMBALI, wanda ya kasance Shima likita ne Anan Mallam Aminun kanon,kuma Senior Ya Nadir ne don ba yaro bane zai kai Shekara 45 aduniya yana mtsayin Constlant ne yanzu,matansa Biyu, ya'yansa Biyar,Bakano ne gaba da baya,yazoma Nadir Daurin Aure Anan yaga Nadira kuma yaji ta Shiga Ranshi har kuma ya gabatar da kanshi kuma nan da nan Nadira tayi accepting dinshi,bayan ya Sanarma Nadir din shima yayi Na'am da mganar,har kuma ya Sanar ma da Abba kuma ga duk alamu Nadira tana son Dr Hambali. ************** Nadira tana kwance Suna waya Da Dr Hambali,Zahra na gefenta tana buga game awayarta taji Nadira na gaisawa da Ya"yan Dr Hambali Abun yabama Zahra mamaki har sai da ta dago tana binta da kallo,ganin yadda take Wani Lallaba yaran kamar Wasu ya'yanta na cikinta tana ji baban ya karbi wayar Nadira ta chanza murya tana mai Shagwaba,Galala Zahra tayi tana bin Nadira da kallon mamaki,wacce Tun lokacin da Zahra ta Fara mata kallon Tuhuma bata bi ta kanta ba sai da Sukayi irin Rabuwar da suka sabayi Cike da kaunar juna,kana ta dago tana kallon Zahra bayan tatashi Zaune tana kallonta kai tsaye tace"Best lafiya..? irin wannan kallon ai sai kisa na kware.." Zahra ta Tabe baki tana Fadin"Wai keda waye kike wannan uwar Kashe muryan..? Ba dai da Tsohon Likitan ba,.? Wani Mirmishin Takaichi Nadira tayi kafin tace"Eh dashi ne,kuma ke kika ga tsoho nidai bangani ba kuma,kinsan Allah best ina Son Dr Hambali sosai kuma da izinin Allah Shi zan Aura.." Kwalalo ido Zahra tayi tana Fadin"Kutumar ubanchan,best kina da hankali kuwa..?tsohon zaki Aura mai mata har biyu da ya"ya..".?."Wani Dirty look Nadira ta sakarma Zahra kafin tace"Eh Shi fa,ko yana da wani Aibu ne,ok sai yanzu nagane ina kika dosa,Saboda yana da mata harda ya'ya ko? Toh ni ba Ruwana da matansa balle ya"yansa Ni da Zuciya daya nakeson Dr Hambali,kuma da Zuciya daya zan Shiga gidanshi matanshi kuma zan basu girmansu a matsayinsu na wadanda ke gaba dani ba Ruwana da kishin Hauka,kishina kenan shine na koyi yadda zan tsaya azuciyar mijina ta hanyar mishi biyayyah da yin Duk Abunda yake so,ya'yansa kuma Suma ya"ya ne Tunda Shine Ubansu kuma soyayyar gaskiya Shine kaso Uba kaso ya"yanshi Shine maganar Gaskiya..." Tafada tana mikewa Zahra data daskare tana bin Nadira da kallon Mamaki,kafin Ta Hadiye miyau mai daci tace"Yanzu ke Nadira sai ki Shiga cikin kishiyoyi har biyu..? Tabe baki Nadira tayi kafin tace"Toh Shine me..? Naga dai kowa ya iya allonshi ya wanke,balle ma dukkansu matan nasu muna waya dasu Anty Umaima da Anty Bilkisu basu da Wata mtsala,kinga Zahra keda zaman gida ke Burgeki gaki gashi ammh nikam kinganni nan nakusa tashi,kuma mganar Auren mai mata da kike mgana in ka tsarkake zuciyarka ka Shiga da Zuciya daya wlh ko mutum nada Mugun Nufi akanka sai ya koma mai.."Daga Haka ta kada kai Ta Fice daga dakin tana wake wakenta ko ajikinta.. Da kallon mamaki da al'ajabi tare Da Nadama Zahra ta Bita,domin ta Fahimci mgana ne Nadira ta sakamata Awasa wandada suka Zafeta sosai,Tagumi ta lafta tana Nazarin Rayuwarta ta baya Sai kawai taji Hawaye suna zubomata,Tasani cewa malika bata taba kulla tanta ba kuma ta sani macece mai kirki sosai ammh son Zuciyarta da mugun kishinta ya Rufemata ido,harta kaita ga Aikata Abunda yazo ya Rabata da mijinta mai sonta da kaunarta,Kuka yazoma Zahra ta Fada kan gado,tana kuka abayyane mai cin Rai Tana juya mganganun Nadira acikin aranta,duk da Nadira bata taba bata Shawaran banza game da zamanta da Malika ba,aamh bata tsammaci zata iya murje ido ta Fadamata wadanan bakake mganuganun ba,Abun ya mata ciwo sosai Wuni tayi kuka tana karajin Nadamar Abunda ta aikata ta kuma dama ace Ana Dawo da hannun agogo baya data Ruga da Gudu ta gyara kuskuran datayi abaya,da yanzu tana gidan Mijinta cikin kwanciyar Hankali Nadira bama zata ganta ba balle harta gayamata wadanan Bakaken mganungun.   _Anan zan dan yi jan  hankali garemu mu yan mata Wadanda muke Waje bamu Shiga daga ciki, ba babban burinmu Shine in mai mata yazo yace yana sonmu,Abu na Farko Shine bazamu Tsarkake Zuciyarmu ba,balle mu barta ta sakama na alheri A"a sai mu bari Shedan ya Shiga Zuciyarmu yana zugamu kan in mun shiga gidan kokarin mu,Mu Fitar da wacce muka samu aciki,bama Tunanin ita ya taji lokacin da mijinta ya auro ki ya kawoki cikin gidan..? Bata kishin Mijinta..? wlh yan mata muna Kuskure Shiyasa Auren zamanin nan kwata kwata baya karko saboda Zuciyarmu ba alheri muke Shiga gidan Aure,shi kuma Allah sai ya barmu da Dubaranmu,daga karshe inta ciki ta tsarkake Zuciyarta Daga karshe ke baki Nasarar Fita da ba, ke ki kori kanki da kanki,wlh mata mu Farka mu chanja munanan Hallayyarmu na zafin kishi wanda bazai kaimu ko"ina ba sai ga Halaka,mune fa da munji wata kawarmu zata auri mai mata ko za"a kara mata Kishiya jikinmu na raawa mu wanke kafa muje mu sameta,in munga ta kwantar da Hankalita Zunciyarta mai kyau ne,sai mu hau cewa koke kina Zaune haka kishiyafa za"a miki ko kuma ke ko yanzu wance me ya'aike ki Shiga Gidan Kishiya kuma kike Zaune baki mike Tsaye ba..? Kuji fa wani zence ..? Toh Ta mike tsaye da me? Wlh da kin yarda da Shawaranta kingama wayo don Maza yanzu Sunfara tsada kuma na garin yanzu Sunyi karanci iskanci kadan zakiyi ya taraki gida wlh da anyi mgana yace Ga mata nan Sunyi Arha kamar ledan pure water,zai maida gomanki wlh,Toh ki natsu keda kika samu Shiga ki sadda kai Ki kuma tsarkake Zuciyarki da Tsoron Allah,ladabi ,da biyayyah ga mijinki kada ki daina,ko aure yace zai kara kada ki zama ballagaza yi kishin musulunci Kina nuna kinfi Shi so ma ya Raya Sunar ma'aiki sai kiga ya Saki jiki,in kina da Rabo ma sai ki tashi da makullin motan Uwargida ta bada Halin kai😂ke kuma ta Waje ko Kinshgo wlh bazai bari ki Raina matarshi Saboda Abunda tayi Darajanta ya karu ko kin Shigo da mugun Nufi sai kiga daga karshe yakoma kanki,Toh Shawarata gareku Shine keda kike Ciki kada kiyi Wasa Damke Abunki don duk yadda kika kai ga Raina mijinki in Wata zata sameshi Sarki zata maidashi saboda gata da so😂 So Tun Wuri ku sauya taku,Domin nima ina kafa kafa danawa kada wata tazo Wuf tamin pdp ta Ture gwannatina na Shiga uku😂,ammh bayan fa na Tsarkake Zuciyata,ALLAH YAYI MANA JAGORA YA KUMA TSARKAKEMANA ZUKATANMU AMEEN SUMMA AMEEN_ Haka Zahra ta Wuni kukanta bamai lallashinta don ko Nadira ta dawo dakin Ta ganta tana kuka,ammh sai ta bata tanka ba kuma harga Allah ta gayamata hakane ta kara ankarar da ita kuskurenta bawai don gori ko Cin Zarafi ba. ************** Karamar mgana Fa ta zama babba Domin Mganar Auren Nadira da Dr Hambali ta Tabbata domin har iyaye sun Shiga ciki Dr Hambali ya Turo magabatansa wajen Abba sun Nemi Auren Nadira kuma yabasu kama daga yadda yayi binciken Shi Dr Hambalin Mutumin kirki ne,An sanya Rana Wata biyar masu Zuwa murna wajen Nadira ba'a mgana Zumudi take Abunda tare da kara Fito da Salo Salo na Soyayya ga Angon nata Dr Hambali. An saka ranar da Sati daya sai ga Jerin matan na Dr Hambali da ya"yansu sunzo gaida momi su kuma ga amaryar tasu Nadira,ku kanku Abun sai ya burgeku yadda suka zo suna wasa da Dariya momi haka suke cemata momi sama momi kasa,Dama Nadira tunkan suzo ta yi musu kayatattacen Tarba,bayan ta tsala wankanta,haka ya"yansu suka zagayeta suna Kiran Anty Nadira kaza,Anty Nadira kaza,haka suma iyayen nasu Duk dukkansu sun Girmema Nadira Nesa ba kusa ba,ammh suna Darajata,musamman ma yaddaa Nadira take basu girmansu Daidai gwargwado Tunkan ta Shigo kuma hakan ya samo Asali ne da adalcin miji da suka samu kuma Dukkansu Zuciyarsu mai kyau ce... Nan suka Wuninma Nadira sai yammah kana Dr Hambali yazo ya Daukesu harda momi da Zahra amasu rakiya, wacce Abun ya tabata,taji dama itama Tun Farko ta kwantar da Hankalinta ta tabbata Malika sai ta mata Abunda Matan Dr Hambali basu ma Nadira ba,momi Dubi biyar tabama yaran suka ki karba sai da iyayansu suka saka baki,itakuma Nadira tabama matan nashi kyautan Turaruka,suma dai dakyar suka amsa sai da Dr Hambali ya saka baki,haka suka rabu cikin farinciki kowani bangare Sun Tafi cike da Kewa da Farinciki,suna Tafiya momi na ganin Zahra da zata shiga daki tana Dauke Hawayenta itako Nadira Kichen ta Nufa domin ta Zubo abinci hayaniya yahana ta ci,Da kallon Tsausayi ta bita kafin ta kada kai Aranta tana Fadin Dama Allah ya kadarra baki da dogon Zama achan Zahra Allah ya baki wani mijin,yakuma sa wannan Abun daya Faru ya zama darasi agarki,agaremu,agareni ni mai Rubutun,da kuma agareku masu karatu Ameen ya Allah. ************* *ZAMFARA*   Cikin Wannan Halin kara'in Soyewar Da Saleem da malika ke tsakar kwasa laulayin ciki yayi ma Malika salamu alaikum,wanda Ranar data Fahimci tana da shigar ciki Wuni tayi amai da zazzabi mai zafi,koda Saleem ya Dawo daga office yaga Halin datake ciki bai jira cewar datakeyi ya kyaleta basai sunje asibiti ba,ya Tada ita Zaune ya saka mata hijabi,ya kama hannunta Zuwa mota. Private hopital ya kaita nan da nan aka Dibi jinita aka gwada sai ga sakamakon ya Fito Malika na Dauke da 2 month preganant,Murna wajen Saleem ba'a mgana bakin nan har kunne,ko kafin su koma gida sai da ya biya yayi musu takeaway Tunda bata da lafiya bata yi girki ba. Malika dai wannan karon Cikin yafi Wahalar da ita Fiye da Cikin Ayda Wacce keda Shekara daya kenan,tafara Tatatan Tafiya Tuni,har mikewa tanayi ita kadai,Kullum cikin laulayi take,ga amai komai taci baya zama,ga Zazzabi dashi take Wuni ta kwana,har asibiti ta kwanta har sau biyu Ammh Abunda sai Addu"a,Duk sai ta rame kamar ba Malika ba,yadda cikin ke Wahalar da ita yasa Ummi tasata Ta yaye Ayda ita kuma tatafi da ita Abuja saboda Wahalan na Malika ya ragu Tunda yanzu Ayda Tunda tayi yawo kuma sai Shigen Rigima ba. Cikin yasa Malika tayi muni duk tayi baki,ga Wasu manyan Pimples da suka Fitomata bula bula afuska,gashi yasata kazanta don in ba Saleem bane ya matsamata ya Shiga da ita tiolet yamata wanka ba,sai Malika tayi kwana Uku batayi wanka ba😂gashi kuma ya saka mata wata irin Masifa Abu kadan sai tataso tana jijiyar Wuya gashi yanzu Duk yadda take Bashi kulawa abangaren Shimfida yanzu ko kusa da ita ya matso,yanzu zata bata rai,balle yace zai Shiga majalisar dinkin Duniya,yanzu zata hau kuka,,Saleem yanzu lallaba malika yake,Saboda ta zama alallaba Auren zamani,saboda yadda take Wahala harta da Abbi yazo Dubata Saleema tazo daga kano tamusu kwana biyu takoma Tunda sun kusa gamawa ana ma mganar Aurenta da Ya Sadiq ne,Su joda dai sai dai suka kira ta waya suka mata sannu,ko fa awayar ne Malika in Masifarta tatashi yi take,merry kam na Hakuri don da ita da Saleem sun Fi kowa ganin Masifar Hajiya malika,mai Cikin yan gayu,shi Acp dayayi mgana tafara Zumbura baki tana kunkuni Duk shi yajamata wahala,😂Toh ya zaiyi Tunda Shi ya kumsa Abunda ke saka bala'in ai ya lallabata arabu lafiya,ko abinci bata ci daga Shasshaka sai awara take iyaci,sai daga baya kuma tafara cin kwaden garin kwaki ,ai Dole Acp Saleem ya jingine buhun gari,😂Shasshaka kuwa maman Abba keyowa tana kawomata,domin ita ke kula da Malika jamgwanm,,in kuma batanan Tasaka merry ta mata wata Rana ma sai an gama ta kawo mata Tature tace bataci😂Shiyasa ACP saleem fa ya ijiye kiyuwa ya zage yana Taimakon Malika don in ya Zauna harta Wajen kwanansu sai yazama bolan Juji saboda Rashin gyara,gashi ta hana Merry Shiga dakinnsu guda biyu,iyakar gyaran nata daga dakinta sai Falo,da kichen..... *SHAKIRA* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *35* .............Malika bata samu Saukin Laulayi ba sai da cikinta yayi kwari yakai kimanin Wata Hudu kafin Tafara dawowa daidai tana kuma kokarin Maida jikinta,Ammh lokacin yana Farkon Shiganshi Malika tayi Rama Sosai kamar Wacce take ciwon Tari,ammh yanzu Alhamdulillah Tafara Maida jikinta ba kamar Da ba. ************** Yau ma takama Weekend ne,ACP SALEEM yana gida bai Fita ko"ina ba,Yana daki ya kwanta bayan yagama latse latsensa ajikin laptop dinsa,malika kuma Tun Safe ta Fita Zuwa kichen Don Jiya dakyar tayi barci sakamakon kwadayin Cin Garin kwaki daya matsa mata Shiyasa tatashi da Safe zata karya dashi. Kwadashi tayi da Kolokuli da kuma Manja kafin ta zo Falo ta zauna kan Kujera taja Filon kujera ta Daura Bisa kafafunta bayan ta Dora Filet din kwadan garin Saman Filo,cikin Zumudi da Murna take Tura garin Daga ganin yadda takeci kasan Abun ya kaimata,don ganin yadda Fuskarta yake Sakin Annurin Farinciki,Rabin Hankalinta naga Talabijin tana kallon Gidan Badamasi atashar Arewa 24 da,Haka kurum take son Shirin Don yana Sata Nishadi. Merry ce ta Fito bayan ta Duka ta Gaisheta,Amsawa tayi kafin tace ta Shiga kichen ta gyara mata Shi ta gogeshi tsab,don yanzu tana kokarin sakawa a tsaftace waje ammh fa ba da kanta zatayi ba,don Malika ko Acp ya Fita Attaka yanzu😂😂. Yadade tsaye daga kofar dakinsu yana Kallonta,Hannuwanshi cikin aljihun Wandonsa,na barci baki mai wani Roba ta kasa,jikinsa kuma babu Riga gabadaya yalwar gashin kirjinsa wanda ya kwanta yayi luf duk ya bayyana,batason da tsayuwar mutum ba balle taji karisowarshi sai dai kawai taji ya Dauke Filet din garin yana kallonta gefe daya kuma yana yamutsa Fuska kamar yaga kashi . Dagowa tayi tana kallonshi kafin ta kwabe Fuska tana Fadin"Kai Mallam don Allah Ka bani bafa kyau mutum na cin abnci ana katseshi kafini sani,kune malamai magada Annabawa.."Tafada tana mai yar Dariya tana kuma gyara Zaman Shegiyar Shimin datake jikinta wanda Cibiyartama awaje,kwata kwata cikin nan ya chanzamai mata fa,Yanzu malika bata iya Wuni da kayan kirki Sai tace Zafi takeji,daga ita sai Karamar Riga da Wando. Da kallo ya Bita kafin ya kara bin garin da kallo yana Fadin"Wai ke baki gajiya da Dura ma cikinki wannan Abun .? Baki tsoron ki haifomin bby,da Tabon garin kwaki.."Yafada yana Tamke Fuska Dariya ya bata Har Sai da ta Dara Tana Fadin"Au dama ana Haifan yara da tabon Abunda Uwa taci lokacin suna ciki ne..? Lalle ko da har dakai ka Fito da Tsiron Danwake don Ummi ta gayamin da cikinka Shine abincinta Shida Wainar Fulawa.."Ta karishe Fada tana Dariya.    Zaro ido yayi yana Fadin"Wai da gaske...?,Dariya Malika ta Kece dashi harda Dukawa,ganin haka yasa ya Bata dankwashi akai yana Fadin"Kazamar mai ciki kawai,wato nine yau na zama cartoon dinki ko..?"Tana Sosa kanta ta kwaremai baki tana Fadin"Wayyo tsakiyar kaina ya Burma wayyo Ummi da Abbi Mallam ya Burmamin tsakiyar kai.."Ta Fada harda matse ido,kamar gaske,dariya Abun ya Bashi har sai da Duka hakoransa suka bayyana Waje... Kusa da ita ya Zauna yana Fadin"Yarinyarnan yar Sharri ce,dan wannan yafa danayi miki ne zaki sakamin kuka kice kanki ya burma,salon kijamin Sharri,in mazaki kukan Jini ne yarinya bamai Cetonki yau.."Jin haka yasa ta bata Fuska ta mika hannu tana Fadin"Ni dai bani Abuna.."Tafada tana kokarin amsa,shi kuma ya maida shi bayanshi yana Fadin"Anki abaki,in kina da karfi ki kwace..."Jin haka yasa ta mike zata tsallaka dayan gefe,shi kuma yayi Saurin mikewa ya daga Filet din sama yana Fadin"In mutum ya isa ya kwata din.."Tsalle ta Fara tana Fadin"Don Allah ka bani,wayyo...!"Dariya ta kamashi ya danne yana Daga mata gira yake Fadin"Au bazaki iya karba ba.? Amshi mana.."Yafada yana sauke hannunshi tayi Caraf zata kama ya dage sama yana Dariya,ganin haka yasa ta Fara Diddira kafa tana kukan Shagwaba,Tanayi yana kallonta yana jin Nishadi sosai yadda take Diran Kafafun ne,Ko'ina na jikinta na motsi yasa wata Sha'awarta takamashi Lumshe ido yayi yana Fadin"Tsaya tsaya..Gashi.."Ya fada yana mikamata Da Sauri ta dakata tana Washe Baki ta mikamai hannu,miko mata yayi ta saka Hannu kenan zaka karba ya Maida bayanshi yana fadin"Da Sharadi ammh.."Jin haka yasa ta Mele baki tana Fadin"Kayi ka Fada,don daga yanzu nadaina Biye maka,sai wahalar dani kake da wayau.."... Yana Dariya ya kai bakinshi Saitin Kunnanta yana Fadin"Don Allah nayi...."Da Sauri ta dago ta kalleshi kafin tace'Kayi me...? Ido ya lumshe kafin ya Shafa saman Nonuwanta har Zuwa saman karamin matashin Cikinta kafin ya gangaro Zuwa kasar maranta yana Shafawa ahankali,kafin yace"Wannan..."yafada yana Kokarin Turamata hannu cikin wandon jiknta,duk da ya kashe mata jiki,Tureshi tayi tana Fadin"lalle naki wayon,na kwada wani yanzu.."Tafada Tana Nufar hanyar kichen din,Ganin Haka yasa ya Ijiye Filet din a bisa kujera ya isa gareta da Sauri sai dai taji ya Dagata sama cak yana Fadin"Ni da Hakkina adnga min yanga,lallema yarinya.."Yafada yana Dariya,itama Dariyan take tana bugunshi akirji tana ihun ya sauketa,shiko bai Direta ko"ina sai kan gadonsu,tana kokarin Tashi ya bita ya Danne,bayan ya sakarmata Nauyinshi,Baknta take kokarin Budewa sai yayi Caraf ya Hade bakinsu waje Daya. *************** *BAYAN SATI DAYA* Aikin ginin Masallacin da makarantan Da malika ta gina Tuni ya kammallah har sun kirata sun Sanar da ita,itakuma sai ta Sanar da Saleem,shine ya bata Shawaran Asanar da jama"a Saboda su samu hallartan Taron Bude Wajen,da kuma Addu"a Ga Daddy,Malika ta yarda da Shawaran Saleem nan aka Fara Sanar da gaddamar da makranta da kuma Masallacin da Malika malik ta gina y'a marigayi Alhaji Abdulmalik Dankasuwa domin Sadakatul Jariya Zuwa gareshi wanda zai Gudana agarin Malumfashi RANAR ASABAR Da misalin Karfe 9 na Safe. Kafin kace kwabo wannan Budaddiyar Sanarwan Hade da Gayyatan ta iske kowa yaji sai ya sakama Malika albarka domin akwai ya"yan masu dashi da yawa wadanda iyayensu ke Mutuwa su bar musu Tarin Dukiya,ammh bazasu taba Tunanin Yi musu Sadakatul jariya ba sai dai Suyi ta Facaka da kudi suna Abunda suga dama,ammh sai Gashi Malikan da ba"a taba Zato ba tama kowa mamaki,kuma wannan ba komai bane,Sila illah Saleem wanda Shine keda kaso 90% wajen Daidaita Rayuwar Malika hartazama Abun yabo da koyi awannan zamanin.    Ranar taron Tun wajen Karfe 8 Suka isa Malumfashi ita da ACP SALEEM dinta,cngam dinta kenan,suna Sanye ne da Shadda mai Ruwan kasa,wacce akallah zatabama Dubu 50 baya Saboda Yadda take Fitar da maiko da yarari,Shi Saleem yayi dinkin Tarzace ne Dinkin Muhammed na Samarin zamani masu ji da kyau da Mukami,Da hulansa Zannah bukar wacce take Kalan,Ruwan kasa ajikinta haka takalmin kafanshi ma Rufaffe ne Mai Kalan Ruwan kasa,hadadde na Fatan Damisa,hakama agogon Fatan Dake Hannunsa,shima Kalansa kenan wanda na kamfanin Rado ne... Itama Malika Dinkin Jikinta Riga da zani ne,Stone work ne,Rigar harpjmp ce,domin ta sauko mata har Gwiwa,sai Babban mayafinta mai kalan Ruwan kasa,da Takalminta mai Dudu Shima mai kalan Ruwan kasa,hakama yar karamar Jakar dake Hannunta,agogon Hannunta kala daya ne,dana Saleem ammh Shi nashi is For men,ita kuma nata For women ne😂in ka gansu sai sun Burgeka kaji kana ta kallonsu baka sani ba,saboda yadda suka zama Abun Burgewa.    Taro yayi taro wanda ya Gudana a haraban sabuwar mkranta Wacce dama masallacin ke kusa da mkrantar,Abbi da Ummi sunzo,hakama Hajiya binta tazo,hakama manyan malamai hadda Dan majalisar Dake Wakiltar Malumfashin yazo,Yan jaridu harda gidan Talabijin duk sunzo daukan gani da ido Bayan Bude taro da Addu"a inda Wasu karin bayanai suka gudana,sai kabama Malika damar mgana,wanda Tunkan aFara gabatar da Taron ta Fara Hawaye, Saleem ne yake Damke da hannunta alamun lallashi,ta Fita ta karbi Abun mgana ammh kuma ta kasa mgana,saboda Tunawa Da Daddyta datayi Abu daya ta iya Fada Bayan ta mika godiya Allah (SWA) sai ta koma mika sakon Jinjinarta Zuwa ga gwarzonta kuma bango gareta,wanda Shine Silan Faruwa komai,shi zata mikama sakon Godiyarta,kuma ta Wakiltashi amatsayin wanda Zai yi bayani Amadadinta,Awajen babu wanda baiji kwallah ba,lokacin da Malika ke Fadin ta Gina wannan mkrantan ne Fisabilla da kuma Sadakatul Jariya ga,Mahaifinta Allah yaji kansa Da Rahma,Kuka ne yaci karfinta,sai da Saleem yazo ya kamata ya Rumgumeta ya maidata wajen zamanta,,taron bai wani jima ba akayi Abunda ya kamata,Malika ta dauki Nauyin malaman mkratan da duk Abunda za"a bukata karatu takeso akoyar kyauta batare da an anshi Sisin kwabon wani ba,Anyi Addu'o'i Da fatan Allah yajikan Daddy,ita kanta Malikar tasha addu"a da Fatan gamawa Da Duniya lafiya kafin Taron ya Tashi bayan an gaddamar da Sunan masallacin *MARKAZUR UMAR BIN KHAD'DAB* Sai Shikuma Mkrantan *MADARASATUL UBAIYU BIN KA'AB*. Basu kwana ba Aranar suka Jiyo zuwa zamfara,Ranar dai Malika Mutuwar Daddy ta dawo mata Sabuwa don da suka Dawo haka ta kwanta akan gado tana kuka mai Cinrai,Sai da Saleem yayi ta lallashi da jikinsa da hannunsa kana ta bar kuka ta koma tana Sakin ajiyar Zuciya,koda Dare yayi zazzabi ya Rufeta Ruf ta kwana tana Nishi sai da Saleem ya tasheta ya bata mgani,kuma yasa Ruwan sanyi bayan ya Rika jiko Towel yana matsa mata jiki dashi,shine taji sauki har kuma ta Samu barci. ___________________    Sannu bata Hana Zuwa sai dai Adade ba"a je ba,an kuma ce Duk Abunda aka Sanyama lokaci Toh zai zo,gashi har bikin Nadira da Dr Hambali yazo,sauran Sati daya inda Shirye Shirye ya Kamkama Aduka bangarorin,Nadira tayi gayyah sosai kawayensu na mkranta da kuma yan uwa da abokan Arzuka,Har Saleema sai dai ta kaima kati da Minti gayyata bayan kuma ta Tura mata ta waya,. Saleema tayi mamakin ganin Nadira tazo har cikin Asibiti ta kawo mata kati  gayyatanta Zuwa wajen Bikinta,nan nema Saleem ke Fadama Nadira itama asanya lokacin Bikinsu ita da Ya Sadiq,wanda nan da Wata uku ne lokacin take gama Housemanship dinta,Tayi Mata Fatan alheri tare da mata alqawarin indai tazo bikinta itama zata Sanar da Dr tasan bazai hanata ba,sun Rabu cikin Aminci inda Saleema ta mata alqawarin zata zo insha Allah. Abun mamaki Nadira bata Sanar da Zahra ta gayyaci Saleema ba,shiko Saleem, Bukar Mada da kanshi ya Kirashi ta waya ya Sanar dashi,bayan kuma ya Turamai sakon gayyata ta waya,anyi haka da kwana biyu Sai ga kiran Nadira,bai da nombarta lokacin don ya Dade da Shareta da nata dana Zahra na Abba kadai ya bari,shima saboda yana kiranshi suna gaisawa ne, kada ya goge Watarana ya kirashi yace waye😂yace baida mutumci,yana dagawa bayan sun gaisa tace itace Nadira,yaji mamaki sosai nan take Sanar dashi mganar bikinta tare da cemai tana gayyatanshi Daurin aure,kuma tana son Don Allah ya Turamata Nombar Malika zata kirata,mirmishi kawai yayi mata yace kada ta damu in ya samu lokaci zai zo,mganar malika kuma ba sai ta kirata ba,Zai sanar ita ammh da Wuya ta samu Zuwa don bata jin dadi cikint jikinta yayi Nauyi.."Cike da Mamaki Nadira kema Malika Fatan Sauka lafiya kafin suyi sallama bayan tace agaisheta,shikuma yace ta gaida Momi,. Ya dade Shuru bayan sungama waya,yana Tunanin wani abu,Abunda yasa bai bata Nombar Malika ba,saboda shi atunaninshi Zahra na wajen,kuma zata iya daukan Nombar Malikan ta kirata,saboda shima kwanaki tayi ta kiranshi baya dauka,daga karshe sai ta koma tana kiranshi Da Rufaffiyar Nomba,Sai da ya kulleta kana ta daina Damunshi.. Sai da yakoma gida yake sanar da Malika sakon Nadira,tayi ta mamaki harta Fadin in Saleem zai barta data jema Momi da Nadira biki suna da kirki sosai,wani kallon lalle ne ma Saleem yayima Malika dole taja bakinta tayi gum,itama din ma jnta baki ne,ammh tasan yadda Cikin jikinta yayi kato kuma Wata 6 kenan ammh kamar wanda zai Fito yau ko gobe,duk ta kumbura musamman kafafunta,Barin ma tayi dogon Zama kafin tatashi duk sai su haye,Sai Saleem ya dawo daga aikin kafin su kwanta yayi mata massges dinsu. **************** Saleema ta cika alqawari tazo bikin Nadira,wanda Sai dai Zahra ta ganta kwatsam suka kama aikama juna kallon mamaki,Zahra ita tafarama Saleema mgana inda ta bata hannu suka gaisa tana tambayanta su Ummi,itako Saleema Karema Zahra kallo take yadda Rayuwa ta Horata Duk ta yi sanyi kamar ba ita ba,Ace yau Ana bikin Nadira ammh Zahra na Zaune waje daya cikin Natsuwa ba iyayi ba hayaniya ba Rawan kai,lalle Ruwa ya Daki babban Zakara kuma Gani ga wane ya ishi wane Tsoron Allah. Saleem bai samu Zuwa Daurin Aure ba,ammh Abbi yazo Har suka Hadu ta Saleema ta biyoshi suka koma Katsina tare,dama tana son Zuwa weeked,amota take ta bama Abbi lbrin yadda taga Canzawar Zahra,Abbi sai yayi amfani da wannan Damar ya dingama Saleema Nasiha wanda suka kashemata jiki sosai takuma yi alqawarin yin amfani dashi... Anyi taro lafiya an kai Amarya Lafiya,ta tare agidan Mijinta dake kusa da Asibitin murtala,,Tsakaninsu da Gidan ya Nadir Babu Nisa,Flat hudu ne Uku na matanshi daya kuma nashi ne,to cikin dayan ne aka Saka Nadira komai dai achan achan sai wanda ya gani,Sai inda ma kayi Ra"ayi ne zaka So ganin wata kishiya,ammh sai ka Wuni a Shashenka bakaga Gilmawar kowa ba,kowa na barayinshi sai ko in An hadu agaisa,kowacce cikinsu ta iya kama girmanta da kuma Salon kishinta yayinda itama Nadira ta iya jan kankanta da kuma Salon Jawo Hankalin Mijinta gareta,ammh batare data Cutar da abokan zamanta ba *Momyn ladingo.."* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *36* ................"Lokacin da Bikin Saleema da Sadiq ya rage Saura Wata daya Takardan Transfer din Saleem ta Fito an maidashi Headquatersu ta Katsina, *POLICE HEADQUATER AIRPORT ROUNDABOUT KATSINA STATE* Murna wajen Malika ba"a mgana dama Tafison su koma katsina da Zama ta gaji da zaman Zamfara. Nan da nan suka Fara parking din kayansu na Sawa,Domin komawa katsina,wanda Malika keta murna har Maman Abba na mata Tsiyan zata tafi ta barta,dariya tayi tace haba ai ko Birnin Sin ta koma suna Tare bazasu taba Rabuwa ba,Sati daya da Samun Tranafer din Suka gama duka parking din Abunda zasu dauka sukayi sallama da makota,shima Saleem din already yagama Sallama da Headquater nasu,bayan ya mika Sauran aikin zuwa ga hannu sabon Acp wato Shugaban wajen na yanzu. Maman Abba ta zama kawar alqawari don da ita suka dumguma Zuwa katsina gidan da Daddy yabama Saleem wanda koda suka isa Hajiya ta tura musu su Dose sun gyara gidan,sun musu abinci,babu Abunda ya samu gidan,domin ana kula dashi Sosai,ga motocinsu guda biyar Nashi Biyu na Malika biyu wanda Daddy ya mallaka musu sunanan a mazauninsu Rufe da Tamfol,dama already makulayan motocin na hannun Saleem.. Malika da Maman Abba sun zaga lungu da Sako na gidan suna yabawa,Tare da jinjinama Daddy irin Kudin daya kashema gidan,komai na Zabinta an saka mata shi,harda Abunda ta Fiso arayuwarta Swimming Fool,Wayyo Dadi kashe Malika Duk da haka sai da tayi kwallar Tunawa Da daddyata ammh bai Hanata Nuna Murnan Tafi jin dadin wannan gidan Fiye da gidansu na Zamfara ba. Maman Abba kwana daya tayi ta juya Zuwa Zanfara wanda Malika da Saleem suka Mata Sha tara na arziki don Ta nuna musu kara Sosai,Malika bata da Wata damuwa yanzu don Gata ga hajiya,ko banza tana jin kamshinta ba kamar da,da ko kamshin Wani na gida bata ji... Saleem ya kai Trasafer letter dinshi Zuwa Sabon Headquater su,yayi wasu cike cike kafin Yafara Zuwa office cikin kwanciyar Hankali,dawowar Malika katsina yasa Hajiya ta dawo mata da Dose suna tayata wasu abun don Cikin malika yana da girma Sosai,Dawowarta katsina yasa tafara Zuwa Asibiti Awo asibitin Federal Medical centar katsina, Tunda da suna Zamfara maman Abba ke Zuwa har gida tana mata,Cikinta Watanshi Takwas yanzu ammh sai ka tsaya ka kara kallon yadda yayi Wani girma yana neman Rufe Malika gashi ya Kumburata Sosai Afuska da jiki,tafiya dakyar tashi Dakyar ammh kuma ahaka take Shirin Tafiya Abuja bikin Saleema,wanda Saleem yayi mata bakam Saboda yaga Malika bata da Hankali baisan ina zata da wannan Tulelen cikin ba taje tabama mutane aiki. Malika batayi Shawara da Saleem ba Ta Turama Ummi Zunzurutun Kudi har Miliyan Talatin,wai gudummuwar bikin Saleema,dana ya marwan Tunda wanchan Lokacin bata bada komai,Sai ga Ummi ta kira Saleem yana office tana tambayanshi Cike da mamaki yake Sanar da ita bai sani ba,yana wajen aiki ammh in ya koma zai tambayi Malikar ita ko koda Ummi ta mata waya tana tambayanta wannan kudin na miye Dariya kadai tayi kafin ta Sanar da Ummi Gudummuwarta,Bakin Ummi bude take Fadin kudin Sunyi yawa,malika tace Allah Ummi basuyi ba,sai dai inda bazaki ki karba ba,Ummi kasa mgana Tayi, illah godiya datayi ta zubama Malika,shikanshi Abbi Dayaji yayi ta mamaki har yayi tama Saleem Fadan yazai bar malika ta dinga Wasa da kudi haka,yakamata ya zauna da ita su Tatauna Abunda ya dace su Dinga yi da Ribar Dukiyarta bawai Shanshanci ba,kaji Abbi😂. Saleema dataji sai gata har katsina Tazo godiya,Malika bata bi takan Godiyar datake mata ba,sai ma Tambayanta datake wata irin mota take so kuma take Sha"awa Saleema bata kawo komai ba tace Vibe motar tana burgeta,gyada kai kawai Malika tayi aiko ko Sati basu da wannan mganar ba sai ga motar Saleema ta iso daga kwatano,Saleema sai da tayi kukam Dadi Saboda Farinciki Ummi da Abbi da hajiya sun kasa mgana,Shikamshi Saleem bai sanin Malika zatama yan gidansu kyauta sai dai yaji lbri daya yi mata mgana Sai tace Gift din Aure ne tabama Saleema da ya Nuna mata kashe Kudin yayi yawa sai da Malika ta maida Abun Fada,tana Tunanin Yanzu don ta bama Ummi yan kalilan kudade,kuma ta Siyama Saleema mota sai yazama Abun mgana,Bataji dadin haka ba,Dole Saleem ya kwaso Rantsuwa da magiya da lallashi ya Dora kafin Malika ta Hakura. Saleem ya Fara Hawa daya daga cikin motocin da Daddy ya mallakamai Tun yana Raye prado din,Na Malika ko ya saka Aranshi zata koma hawa motar kanta,ammh sai dai ta koyi Tuki don Shi bazai yarda da Wani Direba don wannan ai Salon iskanci ne,kai kana nam Bude da baki wani gardi na gane maka mata,kowani kwalliya tayi yana ankare ta madubi yana Hadiyan yawu😂,Ammh bai sanar da ita ba ya bari sai Allah ya Sauketa lafiya. *****************. Biki na Saura Sati daya Bakin lagos suka Sauka Ya marwan da Joda,Ashe joda itama da dan matashin Cikinta har ya Fito,inaga Tun Haduwar Farko tayi gamakatar dashi akofar daki😂Malika na jin Joda tazo itama tace zata Tafi,Saleem yace kadama ta sa rai Joda ta Fita lafiya babu inda zata sai ana gobe Daurin Aure zasu Tafi tare,Ranar lahadi su dawo tare,don bazai barta tana yawo da wannan Abun cikin ba,Dole Malika ta Sadadu da,domin Ta tuna karonsu lokacin bikin Joda,shiyasa wannan karon bata Tada Hankalinta ba,in tayi Duba da gaskiya Saleem ya Fada tayi Nauyi da yawa koda Tama je daWurin babu Abunda zata iya,sai ma karama jama"a Nauyi. Sai Ana gobe biki Malika tazo ita da Saleem wanda Hajiya wannan karon tazo tama Rigasu gaba da kwana Uku kafin suzo,Su merry malika tabari agida Tunda ba Dade zasuyi ba,Koda suka je sun iske ango ya iso Shida tarin tawagansa wadanda ya Saukesu A hotel,shima din ba dadewa zasu yi ba don In anyi biki Ranar asabar lahadi litini zai Wuce da Saleema wajen aikinsa don Bashi da Wani Hutu mai yawa.   Chan su Malika suka iske Ayda an zama yan mata,Ta kusa Shekara biyu,tana Tafiyanta ko"ina Gwanin ban"Sha'awa tana makale da Ummi ko Abbi ko Anty Saleema,ammh saboda wayon data keda shi tana ganin Iyayenta ta makale musu musamman ma Saleem wanda Tunda ya dauketa taki yarda ya Sauketa ko nan da nan chan,Dole yayi Hakuri yana Yawo da ita. Gida ya cika da yan Kumo mata ammh banda maza dayake achan baban gidansu Daddy na kumon za"a Daura Auren,so su Abbi ne zasu Bisu chan wannan karon basu zasu biyo ba,Ranar daurin Aure Tun Safe Su Abbi suka kama Hanyar kumo tare da Saleem da Ya marwan da ango da tawagan abokansa,Sauran abokan Abbi da Wadansu wadanda aka gayyata Duk chan kumo zasu je,sai dai su Hadu achan. Karfe 2:30pm Aka Daura Auren Saleema da Angonta Sadiq,Akan sadaki mafi daraja da kima,basu baro kumo ba,sai da suka tsaya sukayi Walima agidansu Abbi kafin su Dauko hanyar komawa Abuja cikin Rantattsun motocinsu. Abangaren Gidan Biki kuwa ya cika Dakam da jama"ar kumo data Saleem da Jama"ar Ummi da Abbi Allah Sarki Harda yan malumfashin sunzo ma Ummi biki Mota guda,Wanda harda Matan Baffan joda Wato wanda yabada Auren Ba Ummi kadai ba Hatta Hajiya Taji dadi sosai Suka Dinga ina suka saka dasu saboda karramawa Ummi ko bak'inta kawayenta ne lauyoyi kowacce kagani babbar mace mai ji da ado da Dukiya mai yawa kunnawansu da hannayensu suna Kara kaina Zinare da Azurfa kamar ba kudi ake Sakawa Asiya ba. Saleema ma taga jama"ar daba ta taba tsammani ba,Domin yawancin yan Sch din su na Buk yan Faculty su na medicine duk sunzo mata harda Wadanda sukayi Housemanship dasu,A Murtala Aminu kano,Abun mamaki Nadira ta cika alqawari wajen karfe 12 na Rana sai ga tazo Direba Dr Hambali ya saka ya kawota Saleema taji dadin Zuwanta haka ta Rumgumeta tana mata sannu da Zuwa dayake ita da yar Dr Hambalin tazo mai Suna Farha. Takaita har Wajen Ummi sun gaisa ta mata Allah sanya alheri harda 5k dinta kusan Dama Nadira tana da wayau,tasan yadda zata kyautatama Mutum harda wata 5k din tabama Ummi tace inji momi tace ace mata bazata samu Zuwa ba,alhalin Momi da Zahra ma basusan Auren Saleema ya taso ba, Abbi ko hidima tamai yawa Bai kira Bukar Madan ya sanar Dashi ba. Saleema dakin dasu Malika da Joda suke Dakin Hajiya Babban nan takai Nadira,sunyi mamakin ganinta ammh sai suka Shanye mamakin ganin yadda Ta nufosu da dariyarta da komai,gaisawa sukayi suna Tambayan Juna yaushe gamo,Malika sai kallon Nadira take ganin yadda takara kiba da Cika kamar ba ita ba lalle ta samu kwanciyr Hankali. Itako Nadira Malika take kallo ganin yadda cikin jikinta yayi kato,sannu ta mata hartana Zolayanta da ko yan Biyu ne,Malika tayi Dariya kawai domin lokacin tana cikin Takaichi ne domin Kayan ankonsu da sukayi ita da Joda da Saleema da Ummi ,sunki Shiganta dalilin haka fa Ummi tace kada ayi mata Riga da Sikat ayi mata Doguwar Riga ne,ammh kwata kwata taki Shiganta,Har karba Ummi tayi ta kira mai dinki ta sake bashi ya dan Buda,ammh koda Malika ta sa,yadai Shigeta ammh kuma ya matse mata ciki Sosai tana Numfashi Sama sama,dole Ummi tace ta cire,Kuka ne kadai Malika batayi saboda takaichi Dole tana ji tana ganin kowa da kayan kwarai ita sai wata Doguwar rigarta ta sanya mai Roba na kamfanin Armani,ganin haka ne yasa Ummi ta bada Wata atamfa tace yanzu take so a dinkama Malika mai yalwa yadda zata samu ta Sanya.   Nadira sai after la'asar tatafi Malika ko da karfin Hali harda tambayan Zahra Nadira tace tana gida,mirmishi kawai Malika tayi tace agaida mata da momi da Zahra Nadira tace zasu ji,har wajen mota suka Rakota ita da Joda kafin suyi sallama su Fada mota bayan an basu kaya biki,har suka bar Haraban gidan Su malika Na daga musu hannu.   Yan Daurin Aure basu dawo ba Sai After sallar mangarib,sai gasu Sun Shigo,Falon gidan suka baje suna Sauke gajiyan Hanya Yan kumo na musu barka da Sauka,shikuma ango da tawagansa a hotel da suka sauka suka yada zango harda Shi Sadiq dinn,Ya marwan Dai matarsa ya nema ta bashi abinci don Yunwa yakeji koda Saleem yaga Uban garan da joda ta Hadoma Ya marwan kwabe Fuska yayi yana Tambayan Shi ina nashi,Ya marwan na mai Dariya yana Fadin"Ka kira matarka mana,nima ai matata ce ta gatantani.."Jin haka yasa Joda ta saki dariya tana Fadin"Ai ko ya kirata bazai jita ba yanzu tana chan tana kumburin Kaya ya ki Shiganta harda wanda Ummi ta bada aka Dinkamata yau din nan.." kwalalo ido Saleem yayi yana Boye dariyarsa yake Fadin"Ke Da gaske..? Kice yau akwai danja kenan,ai ko bari na noke ya marwan yiman alfarma ci wajen wanda matarka ta kawo ma,Wlh yau In Malika ta ganni na zama Nama.."Dariya suka sakamai Shida Joda,sai ga Ayda ta Shigo da kuka Hawaye Shaba Shaba da majina,Joda ce tayi Saurin Daukanta tana Fadin"A"a Aydan Abbi waya tabaki.."Tana murje ido tace"Annie..."Dan ware ido Saleem yayi kafin yace"Tab yasin sai dai kiyi Hakuri Ayda ta,nima in naje Rama miki ai nakai kaina,Srry kinji zo nan kyale Annie.."Yafada yana mika hannu ya amsaheta Hawayenta yake Share mata yana Fadin"Ke ne Ayda kin cika Rigima kina ganin Annie naki ta zama sai a lallaba ammh sai ki dinga Zuwa kina damunta,Bakije wajen Abbi bane,ko baki ganshi bane.."Kai ta gyada kamar wata Babba kafin ta Washe baki ta tashi daga jikin Saleem ta koma ta Dane Bayan Ya marwan tana Kiran"Dadddi..."Rikota yayi yana Dariya yana Fadin"Aydata,ai na dauka yau ba'a ga Daddin bane.."Rikota yayi yana mata Wasan daya saba yana Cafata sama Tun tana jaririyarta yake mata Haka,harta girma data ganshi zata Nufeshi ya dauketa yana mata Wasa yanzuma Dariya take kyalkyalawa cike da Sha"awa Joda ko wayarta ta Fitar tana musu video tana aika musu da mirmishi Shiko Saleem bai biye musu ya jawo kulan Sinasir din da Joda ta kawoma Ya marwan ya loda uku  A filet ya zuba miyar da akayita da Naman rago,ya ja gefe yana lodama cikinsa don Zahirin Batu yau din nan yasha Yunwa don ko a kumo bai wani tsaya yaci abinci sosai ba Saboda Shi haka yake bai cika Cin abinci agida ba.   Suna cikin haka Sai ga Malika ta shigo da tsinin Cikinta agaba hannunta Rike da Doguwar Rigar da Ummi ta kara badawa aka Dinka mata ammh Still taki Shiganta,Tana Shigowa Fuskarnan ba Annuri ta Nufi Saleem yana cin abinci sai ji yayi ta ta tsayamai bisa kai tana Tura baki dagowa yayi yana kallonta ganin haka yasa ya danne Dariyan dake neman kwacemai yace"Uwar biyu meya faru ne..? Na ganki kuma da Riga ahannu lafiya ke baki sa kayan bane,kiman kwalliyan dashi..?.".Yafada yana kallonta mganar daya Fada kamar ya Tunzurata ne,kawai sai ta Fashe da kuka tana Fadin"Yaushe zan yi wata kwalliya da wannan cikin,Kowa ya saka kayanshi mai kyau ammh banda ni,shine kuma kai kana nan zaune ko ajikin ka.." yana Danne Dariyanshi yace"Ashh,duka sunki Shiganki ne,Kai Abu baiyi dadi ba gaskiya,..."Tana Share ido tace"Wannan ma fa Ummi ta kara badawa akamin Dinkin Sauri itama bata Shigeni ba.."Ido ya zaro yana danne dariyarsa yake Fadin"Kai don Allah..? Kuma sai kace wata giwa ace Abu har an sake dinkawa ammh kuma yaki Shiganki.."Ya Fada yana Dan Ware ido kamar gaske. Dariya ce takama Joda da Ya marwan wanda suke ta Danne ta kada ta Fito Tun Shigowar malika,Wani kallo ta Watsama joda kafin tace"Ke kuma wa kike ma Dariya.."Tafada cike da Haushi Ya marwan yayi Saurin tashi yana Rike Ayda yake Fadin"A"a fa kada ki Wuce kan matata,ga mijinki chan Shiya fara dariyan fa.."Yafada yana nuna Saleem da baki,wanda ke kokarin Rike dariyansa ammh kuma taki rikuwa sai da ta Fito Waje,Malika ta tsaya tana kallonsa cike da takaichi ,mikewa yayi yana Dariya ya Daga hannu yana Fadin"Allah ban miki dariya ba,Srry afuwan haba Malika ta,Haba yar Amanata,Kinfan san Nidake bata baci kada ki bari Ya marwan ya Hadamu fa.."Ya fada yana Dariya wacce takasa tsayawa. Da Haushi ya kama malika sai ta bishi zata makamai Rigar hannunta tana Fadin"Zaka sani ne,wato ma Dariya kake,Tunda ni kamin ciki kabarni da aiki ko,ai akanka zan Wuce yasin kuwa.."Ganin tayo kanshi yasa ya haye gadon yana Dariya sanin dayayi bazata iya hayowa ba,itako ganin haka yasa tayi tsaye kafin ta saki kukan Shagwaba,Ganin haka yasa ya sauko daga kan gadon ya Rumgumeta ta baya yana Fadin. ""Srry bari kuka kinji,nine ko..? Bazan karaba insha Allahu na bar dariyan."Yafada yana Kamkameta ta gefe daya kuma ya zuro duka hannayensa biyu yana Shafa tsinin Cikinta,ya marwan da joda ko Tun Shagwaban Farko suka Fice dauke da Ayda suna Dariyansu Saleem,shiko dakyar ya lallashi yar rigimar nashi tayi Shuru,abinci ma sai abaki ya bata,yayi mata wanka ya Shafamata mai,Ranar dai bata sanya kaya ba ammh Washe gari Dole Saleem ya Fice Zuwa neman ma Malika wanda zai Dinkamata kayan da zai Shigeta kada Ta Cinyeshi danya da Masifarta.😂 Washegari ko Sai da Malika ta Sanya Wani leshi wanda Saleem yasa aka Dinkamata Riga da zani,rigar sai aka Budeta sosai har Zuwa gwiwanta,Dalilin daya sanya ta barshi ya Fita kenan ammh da tace wlh sai dai su zauna tare agida Tunda dai Shi yayi mata Abunda kaya suka Daina Shiganta,😂Saleem yaso su koma katsina Aranar ammh Ummi ta hana Dole suka bari sai monday,yan kumo da abokan Sadiq dai Aranar suka koma. ******************* Ranar monday Tun Safe da karfe 10 am na Safe iyalan IG kabir kumo,suka Raka amarya Saleema da angonta Sadiq suka hau jirgi zuwa garin Abia inda Sadiq din yake aiki acikin masu rakiyan Harda Abbi da Ummi da Hajiya babba da Hajiya binta da malika da Saleem,da Ayda da joda da ya marwan,dukkansu suka rakasu har Filin jirgin Nnmadi azikiwe internationl Airport,suka rabu cike da kunci Saleema dakyar ta saki Abbi da Ummi wanda ta Rumgumesu tana kuka,hakama tama Saleem da Ya marwan Wadanda suma sunji ba dadi musamman ma Saleem domin Shine yafi kowa Shakuwa da Saleema,haka ta Rumgume joda da Malika tana kuka,wani karfin Hali ta rike Ayda wai sai tatafi da ita😂Malika ko tace ta bata Halas malak ta tafi da ita har Saleema ta fara murna Saleem yace Bazai yuyu ba ta bari ta kara girma lokacin,Sunzo ganin gida,sai ta tafi da ita,Dole murnan Saleema ya koma ciki Dakyar Sadiq yajata suka Shiga jirgin Tunda ana ta kiran Sunanyensu,Haka suka dawo gida jikinsu Duk yayi Sanyi musamman Ummi,Motar Saleema kuma Sadiq yace zai aiko Direba yazo ya dauka ya kaimata chan,Tunda achan zatayi Service dinta,kusa da mijinta. Suna dawowa Daga raka Saleema,Su malika sukayi Shirin Tafiya,Ummi taso su tsaya ammh Saleem yaki,wai saboda wajen aikinsa,kuma bashi da alamun barin Malika dole Ummi ta bisu da Allah kiyaye hanya,Wannan karon Saleem yacema Ummi zasu tafi da Ayda bata hanasu ba Tunda yarsu ce,ammh sai Ayda ta watsa musu kasa a ido ta makale Ummi tana kuka Dole Saleem ya kyaleta,da Abbi yaji lbri dariya yayi yana Fadin"Su Saleem masu ya"Toh rigimar me yakeyi ga matarsa chan da wani cikin,ko kuwa Rashin kunya yaran zamani.."Dariya kawai Ummi da ya marwan sukayi tayi Sanin Halin Saleem din da Shi kanshi Abbi. Tare da Hajiya Binta suka Wuto katsina sai aka bar gida Daga Joda sai ya marwan wanda sai Wani Sati zasu koma Lagos din,Su malika sun isa gida lafiya,hajiya kuma har gida suka kaita,koda suka koma su Merry sun gyara ko"ina na gidan,Saleem baima Zauna ba office ya wuce saboda an kirasa yana da baki itako Malika Suna dawowa Ta fada gado tana barci don ta gaji ga bayanta ya Rike kafarta kuma ta haye Saboda Zaman mota. _Naga alaman yan group din Hafnan and Janaf paid group, da ku da Yan Malika malik paid,kun fara gajiya da Malika,kundaina nemanta balle zuzuta da Sharhi😂Kodon kunga tana muku bankwana..? Karku damu Soon zamu dawo mu Daura ,Bansani ba ko kafin nayi muku *ZAMAN GIDANMU* mai cike da kunci,ko kuma sai bayan na kammallashi ne zan yi muku *NANNY* _Mai Reno_ Free wanda sadaukarwa ne gareku masoyan kwarai Malika malik paid,da kuma Janaf and Hafnan Paid,ALLAH YABAR KAUNA DA ZUMUNCI NA HAR ABADA.."Janafty tana alfahari daku.._ *SHAKIRA janafty..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *37* ............."Malika Da Saleem sun Cigaba da Renon cikin Malika wanda ya Shiga Wata na Tara ammh kuma yayi girman gaske gashi ta kara Hauhauwa in ka kalleta Sau daya bazaka ce Malika bane Dole sai kara kura mata ido kafin ka tantance itace ko ba ita bane. Gabadaya ta rame tayi baki ta Rame,gashi Ta kumbura tayi Suntum,Tashi dakyar zama dakyar,shikanshi Saleem din Hankalinshi take yake da Tsausayin Malika,Sun Riga sun gama Shirin Haihuwa ganin Watan Haihuwan ya Shiga,ammh kuma haihuwan Shuru har Cikin Malika Ya haura Wata Tara ya Shiga na goma,ammh Haihuwa Shuru ganin hakane yasa Ummi tace Hajiya binta tazo ta Dauki Malika suje asibiti aduba agani in Haihuwan ta garara,kawai ayi mata operation,saboda wahalan tayi yawa ko itama Malika ta Wuta da wannan Wahalan. Da Ummi ta kira Saleem Tana Fadamai Shawaran data yanke,sai ya nuna bai yarda A kai Malika asibiti aje akwakulo mata Nakuda ba,Su kara Hakuri Zuwa nan da Sati daya su gani,in bata ji komai ba,kuma bata Farajin Nakuda ba,sai a tafi asibitin ansan yadda za"ayi,Ummi bata ki Shawaranshi ta bar mganar haka,ammh kuma har Satin ya Shude wani ya Shiga Ba mganar Haihuwa,Dole Saleem ya yarda ya Dauki Hajiya Binta ita da Malika suka Nufi Asibitin datake awo Wato Federal Medical Center katsina. Suna zuwa aka shiga da ita dakin Scanining,nan suka iske yan biyu ne acikin malika,don sai alokacin Allah ya gwada musu don ko da take Zuwa awo suka mata scaning Namiji daya suka gani Allah ya hanasu ganin dayan,dama toh ai karambani ne,Allah kadai yake da ikon sanin Abunda zai Faru yanzu ko anjuma,kuma Shike da ikon ganin komai,kuma Ya zartan yanzu kuma ya Faru,likitoci kawai wani lokacin Allah na basu dama ne,ammh sudin ba Allah bane basu isa su ga Abunda ya Halitta acikin mace ba,sai dai in Dan Allah yaso ya gwada musu da kanshi. Yan biyu ne,ammh daya ya jirkice kafarshi tana wajen kan dayan,Shi dayan yana so ya Fito,ammh kuma kafafun dayan daya chanza wajen zama ita ta tokoreshi,koda dayan zai yi yunkuri Fitowa sai kafar dayan ta tokoreshi ta hanashi kuma shima so yake ya Fito,ammh kuma ta kafafunsa Tunda Ya jirkice,lalle ikon Allah,Shine Dalilin Daya sa Harta Wuce wattanin Haihuwarta bata haihuwa ba,da ace ta kara wasu kwanaki in suka yunkuru zasu Fito gabadaya zata iya Rasa Ranta suma yaran koda zasu Fito may be suma ba'a raye ba saboda sun Jigata aciki sosai... Bayanin da Dr yayima Saleem da Hajiya kenan ya kuma umarci Saleem daya sanya hannu yanzu zasu Shiga da Malika dakin Tiyata Domin Cetonta ita da Abunda ke Cikinta,kuma suka bashi Umarnin yaje ya biya kudin aikin yanzu yanzu,Jikin Saleem na Rawa ya Rattaba hannu kafin ya kwashi Gudu yaje ya biya kudin Aikin da za"a ma Malika,Cikin lokaci kadan suka gama Shirya malika cikin kayan Tiyata suka gungurata zasu Shiga da ita dakin Tiyata,Lokacin Su saleem suna wajen Da hanzari ya karisa ga Malika ya riko hannunta haka ke Zubomata sha,ya sanya hannu yana Sharemata yake Fadin"Stop crying kinji za"ayi aikin lafiya insha Allah kinji.."Kuka ya kwace ma Malika ta sakeshi tana Shesssheka take Fadin"Mutuwa zanyi Mallam,ka yafemin don Allah.."Abunda ta Fada ya Kashema Saleem da Hajiya gwiwa bai samu zarafin mata mgana ba,Suka gungurata Zuwa dakin Tiyata wanda Hannunsu dake sarke da juna ya Rabe,har aka Shiga da ita suna kallon Juna Malika na Fitar da kwallah.. Kai Saleem ya Dafe yana kiran Sunan Allah,haka yaji Duniyar tayi masa kunci Bai Saurari Hajiya dake Fadin ya bar Damuwa Malika zata haihu lafiya,cikin mota ya koma ya Dafe kanshi da Sitiyarin mota yana Fidda Numfashi sama sama yana kallon idanuwan Malika suna Fitar da kwalla,tsigar jikinsa ne ya tashi sai yakeji kamar kallon bankwana tayi mai,Saleem har sai da ya Fitar da hawayen Tsausayin kanshi dana Malika,nan cikin motan ya cigaba da zama don baida kuzarin komawa cikin Asibitin yana ji wayarsa dake cikin aljihu tana Faman Ruru ammh kuma yakasa sanya hannu ya Cirota balle yaga kowaye mai kiran nasa. Ummi ko dagachan Bangaren Hankalinta amatukar tashe yake ganin Tana ta kiran Wayar Saleem bai dauka ba,bayan kuma sunyi waya dashi Sanda zasu kawo Malika asibiti ganin bai daga kiran nata bane yasa ta maida akalan kiran nata kan Hajiya Binta ita ta dauka ta mata bayanin Abunda ke Faruwa,hankalu fa sun tashi sosai don nan Ummi take Sanar da Abbi wanda Shima hankalinshi ya tashi ammh sai suka barma Allah komai suka koma mata Fatan Allah yasa ayi aiki lafiya kuma afito da kai lafiya. Shudewar Awa uku likitocin da suka Shiga da Malika sukayi kafin Su Fito,Kowanne Fuska ba Annuri Hajiya dake zaune awajen,tayi Saurin mikewa tana Tambayansu ya Malika..? Anyi Nasara kuwa..? Basu samu bata amsa ba illah tambayan Saleem da sukeyi ganin haka yasa Hajiya Binta tayi waje da Gudu,aharaban asibitin ta tsaya tana Neman Saleem bata ganshi ba,har masallacin shashen maza ta leka ammh bata hangoshi ba,ganin motarshi a parking space ne yasa ta karisawa ta Gudu ta kwankwasa glass din gaban motan tana Fadin"Saleem,Saleem malika.."... Kansa na Bisa Sitiyari Barci ne ya fara dibanshi Harda Mafarkin An Fito da Malika ta Haihuwa lafiya kamar amafarki yaji buga glass,shi ya tadashi A Firgice yana bin inda yaji karan da kallo,dayake motar Tinted ne na waje baya ganin na ciki,shi ya Fara ganin Hajiya,ganin yadda Fuskarta ya Nuna damuwa ne yasa ya balle murfin mota ya Fito yana Fadin"Gani Hajiya lafiya..? Sun Fito da Malikar ne..? Hajiya Bakinta na Rawa tace"Eh nemanka suke.."Jin haka yasa ya Runtuma da gudu Zuwa cikin Asibitin Jikinsa na Rawa saboda Fargaba,itama Hajiya ta takemai baya. Yana zuwa kofar Theater Room ya Gamu da likitocin bai jira cewarsu ba yafara Fadin"Hop d Operation is Sussesufull,...? Kallon Juna Sukayi kafin wani daga cikin Likitocin ya Dafa kafadanshi yana Fadin"Yes..d bbys are in good condition buH...."Saleem yaji Zuciyarsa na lukude ya Warce kafadansa daga hannu Dr yana Fadin"Buh waht...? Yafada Duka idanuwansa suna waje... Kansa na kasa yace"Buh u lost her..."Zaro ido Saleem yayi cike Da firgici ya cakumo Wuyar wanda yace Malika ta Rasu yana Fadin"Kutumar ubanchan,Matar tawa ce zaka ce min bata,kana da Hankali kuwa,Wlh sai na kasheka nima..."Yake Fada da alamun ya Fita daga hayyacinsa,Hajiya data Fahimci Abunda ya Faru ta dora hannu aka tana kuka tana Fadin"Innalillahi wa'inna Alaihirraju'un.."Sauran likitocin ne suka Rike Saleem suna Neman rabashi da Wuyan wanda ya shaka,ammh sai Fuzge Fuzge yake kamar mahaukaci yana Fadin Shima sai ya kasheshi indai Bai Fitomai da matarsa ba. Wani daga cikin Dr din ya Riko Kafadun Saleem da karfi yana Fadin"plz mrs man Cool down We know ur Feeling.buh am so srry to say u Wife iz Dead,we are Srry..."Zuru Saleem yayimai da ido yana kallonsa kafin yaji Duniyar na juyawa dashi kafin kace me, ya Sulale zai Fadi asume Dr din ya Rikeshi yana kwalama Nurses kira,nan da nan sai gasu da gadon daukan Marasa lafiya suka daukeshi Suka dorashi suka Shiga dashi wani daki. Wata Nurse ne dake Dakin Tiyata ta Fito da Sauri tana Fadin"Sir She iz Breathing,..."Zaro ido sukayi atare kafin su Rankaya cikin dakin da hanzarinsu cikin gaggawa,shiko Saleem taimakon gaggawa akabashi kafin asamu ya Farfado aka yimasa alluran barci,Hajiya dake waje ban da kuka da Salati Babu Abunda takeyi tana cikin wannan Halin ne sai ga wani likita ya Fito daga Tiyata Room din daga ganinshi Musulmi ne,kallon Hajiya yayi yana Fadin"Mama kuyi hakuri da Abunda ya Faru lokacin da suka Ciro bbys din dake cikinta sai Numfashinta ya dauke,so sun zata ta rasu buh yanzu Numfashinta ya dawo komai ya Daidaita mun mata alluran barci zamu Kawota dakin Hutu ita yaran ta samu Twice,Duka Maza..", Hajiya Binta Tana washe Baki take Fadin "Alhamdulillah..Allah mungodemaka.."Take Fada tana Share kwallah,Daidai lokacin kuma wayar Ummi tashigo wayarsa nan da nan Hajiya ta daga bayan sun gaisa take tambayanta ya ake ciki..? Nan Hajiya Take Sanar da ita komai,Ummi ta Girgiza kai Tana Fadin"Ina Shi Saleem din..? Hajiya tace"Sun Shiga dashi ciki suma yayi lokacin da sukace Ba malika.."Ajiyar Zuciya Ummi ta sauke Kafin tace"Allah ya sauwake Allah yabata lafiya ya kuma Raya Abunda aka samu,Da safe muna nan Tafe.." Dahaka sukayi sallama da Hajiya nan take Fadama Abbi Abunda ke Faruwa,ga murna ga damuwa sun tattara komai sai gobe in sunje sun gani kafin kace kwabo Haihuwan Malika ta zaga dangi,shiko Saleem sai da Daddare ya Farfado inda ya samu lbrin Malika bata mutu ba,sai lokacin yaji Abunda yamai Nauyi akai ya sauka,itako Malika bata Farfado ba sai Washegari,Dayake Hajiya ta kwana da ita Shikuma Saleem yakoma gida,Tana Farfado Abunda ta Haifa ta Fara Tambaya inda Hajiya ta mika mata su Duka biyu,kukan Farinciki Malika ta saki ta kamkame yaran,Kafin ta tambayi Saleem nan Hajiya ke Sanar da ita Abunda ya Faru,wani Farinciki ya Ratsata ganin Har Suma Saleem yayi Saboda Ance ta Mutu lalle ba karamin So da kuma muradi Saleem ke Mata ba. Saleem Sai wajen 10 yazo,shi yazo musu Abun karyawa,shida merry yazo Saboda tataya Hajiya zama,Lokacin dayayi Arba da Malika agaban Hajiya ya Kamata ya Hadata ida yaran ya Rumgume yana Hawayen Farinciki,Malika na mai Dariya mai Suma,Keyarta ya make yana Fadin"Waya ce miki na suma..? Inda ace kin Mutu da nima binki zanyi Amanata,.."Kansa ta Shafa tana Fadin" Bazan Mutu ba Mallam,ina tare dakai Abadan,dakai zan rayu da kuma kai zan mutu.."Bakinta ya Sumbata cike da So Da kauna,hajiya dai Tuni tayi waje don Saleem dare dare kan gado yana ta Sumbatar Yaran,,yana kuma Hadawa da uwarsu,yana kuma ma Malika dariyan wannan karon ma yaci gari domin Gabadaya yan biyu kamaninshi suka debo,wannan karon ma Farar Fatar Malika kadai suka debo ammh har Shape din hancinsu,irin na Acp Saleem ne. Ahaka su Ummi suka iso suka sameshi sai da Ummi ta Faffatakeshi waje kana Ya Fita,harda Rigimammiya Ayda aka zo,aiko nan taga Bbys ta makale tace bazata koma ba,Ummi tayi tayi Ammh Ayda ta makalema Malika tana Santin Kannenta,Dole su Ummi suka tafi suka barta wajen Hajiya,washe gari sai ga yan Malumfashi sunzo Duba Malika ,mota guda basu jima ba suka koma Dama ganinta sukazo yi,washe gari kuma sai ga yan kumo suma mota guda sunzo Duba Malika da zaratan magidantanta,wanda taji sauki sosai kamar ma ba"ayi mata aiki ba.. Joda ko da Saleema awaya suke kira suna ji kamar suyi tsalle suzo,saboda Zumudi ammh kuma duka mazajen nasu sunce sai sun Duba sun gani,ammh da Wuya su barsu suzo,Kwanan Malika 5 Aka sallameta ta koma gida Tunda taji Sauki sosai Dole Hajiya ta Dawo nan tana Kula da ita su merry na taimaka mata Tunda hidimar dayawa gata yan Biyu gata Ayda wacce ake Daga da ita sai ta Dauki Yan biyu,kuma ba dabam dabam ba,a"a so take abata ta dauka Duka biyu alokaci daya in ance bazata iya ba,sai tasaka kuka sai Babanta yazo ya Dauketa yayi ta lallashi ko yabata wayarshi ya Shigan mata game take Hakura.. Awannan karon ma Saleem ya Shirya Sunan Kece raini,Domin Sa guda Za"a yanka banda Raguna uku da kaji,Abun fa sai wanda ya gani,Ana gobe Suna Saleem yayima Yara Huduba da *KABIR* Da kuma *ABDULMALIK* Sunan daya Dadala Ran Malika Sosai Ganin yau ta Haihu da cikinta tama Daddylove takwara Shida Abbi,Abbi ma yayi murna Shima yayi bajinta Sosai,Maman Abba ma tazo ana gobe suna,Saleema ce Kadai ta samu Zuwa Joda kam tayi nisa dayawa,bama haka ba cikinta ya Tsufa mijinta yace baigama mata Shiri ba so yake in tazo to bazata koma ba sai bayan Ta haihu Dole ta hakura.... Sunan Zaratan mazan na Saleem an Shiryashi Domin Tun Ana gobe sunan Mota ta dinga sauke duk wani Nau'in Lemon sanyi na Sha da kuka sani sai da aka Saukeshi,duk kuma wani Ruwa na kowani kamfani Shima an Saukeshi Domin Taron gobe,Su Maman Abba da Saleema ko Tun daren Ranar suka Dinga Soye soyen Naman Raguna da kuma kaji,Domin bakin da zasu zo gobe yan Suna Duk da dai Duk yan"uwa ne da abokan arziki,Wannan karon ma Ummi akwati Hudu tayi na malika daya na Zaratan magidanta kuma Kowa daya daya,hakama Abbi yayi musu akwatina Shake da kaya na malika dana Takwaranshi da kuma mai Sunan Abokinshi. **************** Washegari Ranar Suna,Baki na nesa dana kusa Duk sun Hallara Jama"ar kumo ma sunzo,Jama"ar Malumfashi ma sunzo mota guda Domin taya Saleem murna Shida Malika,wacce ta kece cikin Shigan ta alfarma Kafafunta da hannayenta sun Dauki Shekin lalle ja da baki wanda yakara Fito da ita sosai,yan biyu ko Wadanda akeyima alkunya da AYYAN DA AYRAN suma an cakare su cikin kayan alfarma gwanin ban'Sha'awa wadanda suke kama da Ubansu sak kanar yayi kaki ya ijiye,Mganar Abinci ko,Reataurant ne guda Saleem ya yi odarsu suka zo suka baje kolinsu Kowani Nau'in abinci akwai su Awajen komai kake bukata aikwaishi Sai dai kaje ka diba son Ranka babu mai hanaka ko yayi maka iyaka. Wajen Misalin karfe 12pm sai ga Motoci har biyu cike da Mata,Da farko anyi mamakin ganinsu ganin yadda suka ci angonsu cikin wani Leshi mai Ruwan Hoda wanda keda zanen kwalliyan green ajiki,kowacce ta daka Uban Dauri ta chaba ado ba Raini,Akallon Farko zakayi musu ka gane ba Raini don ba yaku bayi ba ne😂,Sai bayan Sun Shiga ciki ne,Malika ta gansu sai fa Ta tuna su, Masoyanta ne daga *HAFNAN AND JANAF PAID GROUP* da kuma yan Amanata wato *MALIKA MALIK PAID GROUP* ,Nan da nan ta karbesu hannu bibbiyu ta hadasu da Maman Abba da Saleema tace aware musu daki na musamman,saboda bakinta ne,nan da nan ko aka Shiga ina aka saka dasu,Haka aka dinga jera musu Nau"o'in abinci da lemuka Kala kala gabansu bayan Uban Naman Rago soyayye da kuma Naman Kajin da suka dinga yi musu hy acikin manyan Filet din da aka Jirke agabansu,Tuni Su Sahiba Sarkin kwadayin Naman kaji,Tafara Hadiyan yawu kamar wata mayya ta mika hannu zata dauka Uwar dakina Chubado muhmmed ta kabe mata hannu tana Fadin",Haba hafsy meye haka ki bari mana za"a baki kina Abu kamar baki taba ganin naman kaza ba,don Allah karki badamu mana Acp Saleem ya Shigo yaganki kina Halainiyar Naman kaza ya Rainamu.."tafada cike da yanga ammh itama cikin Zuciyarta da bakinta kwadayin Naman ne ke cinta ammt ta danne,itako Dotata ladingo kusan Abunka gamai ciki,😂😂miyanta har ya tsinke ta Kafe Ferfesun kayan cikin dake wajen da ido,Sisinah Aisha alto ganin haka yasa ta matso mata da kwanon gabanta tana Fadin",Ci Abinki Diyarmu Shalelenmu ni da Janafty,kada ki kwari Jikanmu😂Fadin haka keda Wuya Dota ta fara Sharban kayan cikin nan ko jinta tasu Maman kausar da Fati sadiq da suke mata Tsiya bata yi ba,Su Nazeefa ko da Ummu bilal,ummu bilal2 da Ummi haneef,sune manya sai wani manyance suke suna tsara komai,ammah Abun mamaki da sun Fakaici indon mutane sai su Tura hannu cikin Farantin Nama su debo su Tura cikin wasu manyan jakunkunan da suka zo dashi kamar zasu saka kan mutane Ashe saboda suyi Satan Nama ne😂. Hajiya Zuwaira ko da Kawa juwai,ko Suna barayin lemuka,sunfa sha har sunkusa amai ammh haka suka dinga Turawa har suna guzuri ajaka toh Abun ne dayawa Shiyasa babu Wanda yabi takansu,su Aisha amarya,su Aisha musa,su Amsopy,Asma"u Bafarawa,Asmau shehu,asmeey,Aisha usman,Bbj da bilkisu sani kuwa harda Fadan Fride rice,yadda kukasan basu taba ci ba😂Sai da su Dijah Abdul da fatima Musa,ta niger,fati sadiq,Fatima Xahra da fee sai jikar hajiya,haleem Sweetheart dina,jidda lawan,khadee Noor,Khadija muhd manga,khadija usman,khadija bashir,momy h,mmn Nabila,,mm Teema,mmn Useey,mmn kausar,Mmn bby,mmn khairat,mmn Nazeer,mmn Rabia,mmn Ummulos,mmyn Abdul,murja bakugu,suka rabasu Alhalin suma kowacce ta cika jakanta da Awaran kwai da aka kawo musu,Sata ce taci sata,ba wacce bata sata tayi cikin Jakanta dashi ba,ammh suna raba wasu fadan Hinkafa😂😛,Ai Ba Abun Haushi sai yadda su Besty ta da Nucy girl,Rafi"atu,yar Fulani,Saleema Hamza,Sardiya,Ummi,my Azeeza,deejart,Fatima garba,Hadiza,mmn basma,mmn sayeed,mmn Baraka,Malika masoyiya,mmn Amira,mrs umar,Durlig Rukayyah,mumy Halil,Rouky,Suwaiba,mmn Sadiq,Nafisa,mmyn sani,mrs zainab jega,Fatima umar uwaisu,Shafa yola,wasila,Rafiatu s Rimi,Khadijat usman,Bilkisu Duwan,Suka Dinga bi suna kulla Duk Abincin da suka rage aleda suna Turawa ajaka da Nama ne,dasu lemuka,da Zuwaira da Nazeefa,da su Ummi bilal sukayi musu mgana cewa sukayi abarsu su jida,gida babu,bikin irin na Malika kuma sai Rabo ya Ratsa makota kuma sai daidai😂😂Sun dai ci sun sha don ko Sunan yan biyu sun fa goge Wuya Da Naman kaji Abun ba Dama. Sai dai kuma da suka tashi Tafiya basu bar Malika haka ba,Kowacce sai da ta bata dan Abun suna,kafin suyi musu sallama su Tafi bayan kowacce ta cika jakanta da abubuwa,Malika ta rakasu har Wajen mota tana yi musu Fatan Sauka Lafiya,amotarma ma fa Allah ya tsare da anyi Dambe don Mmn Sadiq,ce da Sahiba suka so su kasa hali kan cinyar Naman kaza da Sahiba ta sato acikin Sikat dinta😂Sai da Direba ya tsawatar yace kada wacce Ta kuskura tamai Fada amota kana kowacce ta Shiga taitayinta.😂😂😂😛😛😜😜😜 Anyi suna lafiya angama lafiya Washegari yan KUMO da yan Malumfashi suka koma,suma cike da kayan arziki,Suka tafi suna Malika da Saleem fatan alheri da Fatan Allah Shi raya Ayyan,da Ayran. *Momyn Ladingo..* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *38* ..............."Su Maman Abba da Saleema su kadai aka bari suka cigaba da soye soye basu Tafi ba sai da komai ya kammallah,Suka taimaka aka gyara gidan kana,maman Abba ta Wuce zamfara ita kuma Saleema tatafi Abuja ta kwana Washegari zata bi jirgi Zuwa Abia. Ita kuma Hajiya, Ummi ta roketa Kan ta Zauna ta dan kara ko Sati daya ne kafin goggo Hadiza tazo wacce tatafi minna An mata rasuwa,sai ta dawo kana zata zo ta zauna Da Malika uwar mazaje. Hajiya ta Zauna da Malika har Na tsawon Sati biyu tana kara kula da ita da Kuma su Ayyan Duk da gasu Merry suna kokarin Taimakamata,sai Ranar ta cika kwana ashirin da Hudu kana goggo Hadiza tazo,sai Hajiya Ta koma gida ta barta tana Kula da Malika wacce ta warke kamar ba ita ba. ****************** Tun Malika na kwana 36 Da haihuwa jini ya Dauke mata tayi wanka Tafara Sallah Ammh Bata bari Uban gayyah ya sani ba,domin taga take takenshi so yake ya barta da Abun kunya agaban Goggo Hadiza,Don Tun Satin daya wuce yake damunta da ya kosa ta Fara sallah wlh a daddafe yake yayi kokari ta taimakeshi,Bata nuna mai komai ba,Sai Ta nuna mai Data Fara zata mai mgana,sai dai wani lokacin ta Saci jiki taje dakinsa ta Dan mai Dubaran,su na mata ammh Duk da haka bai wani gamsuwa shi burinshi yajishi Cikin babban Fada😂.   Ga wannan karon su Ayyan da Bala"in kuka suke da Tsotse,bata da lokacin kanta,data samu sararin zuwa dakinsa ko Dadewa baza tayi zata ji kukansu da kuma kiran goggo Hadiza,Da kuma ta Fahimci Dakinsa  Taje Sai goggo Hadiza ta kama mata Fadan zatayi kazantattacen jego matukar ta biye ma Namiji kaita zai yi ya Rabo wlh,wato yaga jiki yayi Taushi ,shine ita zata biyemai Shiyasa wani lokacin ko ya kirata bata Zuwa,sai tace mai su Aryan na Rigima.     Yau da Wuri ya dawo yana Shigowa Direct dakin Malikan ya Shiga,yana Shiga ya ganta tana sallar mangariba,,galala ya tsaya yana kallonta,yana mamakinta domin Jiyan nan ya Tambayeta yaushe zata Fara Sallah ,tace bata sani ba,akofar dakin ya coge yana binta da kallo itako ta jikin madubi ta hangeshi sai da gabanta ya Fadi,Sai ta Daburce ta idar da sallar ammh sai ta sake kabartawa Yana kallonta bai mata mgana ba, illah takowa dayayi ya zauna agefen gado batare da yayi mata mgana ba. Tun tana mai karyar Sallah harta hakura ta Sallame tana Raba ido,bata yarda sun Hada ido ba,tayi zaune tayi Zuru gabanta na bugawa,Ta gefen gado ya kalleta kafin ya saki Siririn mirmishi kafin yace"Kin idar da sallar..? Na zata sai gobe zaki idar..? Shuru Malika tayi tana wasa da Gefen Hijabinta,ganin batayi mgana bane yasa ya mike yana Fadin"Ina ayda ko tana wajen goggo ita Da su Aryan..? Da kai Malika ta bashi amsa,Dariya ta kamashi yayi yana Fadin"Kin zama kurma ne..? Ko Azumin mgana kikeyi..? Bata dago ba balle ta bashi amsa,kofar ya isa ya sama key kafin yazo ya Tube karamin Towel ya daura iya kugunsa ya Fada Wanka tana binshi da kallon mamaki,tana zaune awajen har ya Fito yana kallonta Shima ita yake kallo kai Tsaye yace mata"Kinsan Hukuncin macen data kema mijinta karya..? Ya fada yana goge Sumar kanshi da wani karamin Towel,Kanta na kasa tace"Karya kuma...? Dan mirmishi yayi kafin yace"Eh kin min karya kince baki Fara sallah ba,saboda kada Nameni hakkina ki bani ko Malika..? ya Fada cikin wani yanayi,Mikewa tayi jikinta yayi sanyi kafin tace"Wlh ba..."Shiii...Is ok,ai bazan Nema ba Tunda na Fahimci Guduna kike,bakomai Zan zauna ahaka ammh ki sani in na kasa control din kaina har na Fada wani Hali kome ya Faru kece Sila.."Yafada cikin son Tabbatarwa,kafin ya isa gaban Merro ya jawo lotion ya Fara shafawa. Jikin Malika yayi Sanyi da azama tataka zuwa gareshi kawai sai ji yayi ta Fadaomai jiki ta kamkameshi ta haya,Hannu yasa yana so ya bambareta daga Rumgumar da tayi mai,ammh ta ki sakinshi suka Fara kokawa,ranshi bace yake Fadin"plz Ki sakeni kafin Raina ya baci,badai jikinki ki keman Rowa ba,ki jika kisha,ni bazan yi zina ba,ammh kisani zan karo wacce ko acikin wani hali na nemeta zata bani kanta.." Jin haka yasa ta fashe da kuka tana kara Rikeshi Kamkameshi tayi ta Zuro da hannunta ta cikinshi tana mai Shesshekan kuka cike da Shagwaba,Shuru yayi mata yana bin Fuskokinsu ta jikin madubi da kallo,Kara Hade rai yayi yana Fadin"Wai ina wasa dake ne Malika,i said leave my body ko..?Narkemai takarayi kafin tace"Wlh bazan tashi ba,ni da jikina,kuma Shikenan daga kuskure kadan sai ka yankemin Hukunci baka iya tsayawa kaji Uzurina.."karamin Tsaki yaja kafin ya waigo da karfi ya kuma sa hannu ya Ture malika baya sai ta Fada gefen gado yaraf,Arazane ta dago kanta tana kallonshi kafin ta samu Zarafin mgana yace"Bana son Jin komai daga bakin plz leave me olone,indai kan ki bani hakki na ne,Malika kiyi ta Rike kayanki bazan kara ce miki komai ba Do wht ever u want i dont care.."Yafada kafin ya isa jikin Wardrope ya dauko Wasu Riga da wando na kamfanin Armani,ya saka yayi cumbing din kansa ya Fice bai kara kallon Inda Malika take ba,ta kallon ta bishi kafin ta kwanta bisa gadon Tana Fashewa da kukan takaichi da cin rai,Shiko Ficewa Yayi daga gidan gabadaya,har wajen 10 da Malika taje dakin Goggo Hadiza ta basu Aryan Nono Saleem bai Shigo sai hankalinta ya tashi Zuciyarta ta Fara mata wasu Tunanen ko dai wajen Wata yar iskan karuwan yaje..? Tuni Taji Hankalinta ya tashi,ammh sai tayi saurin Kauda wannan Tunanin Saboda tasan Halin mijinta baya shaye Shaye baya Neman mata,ammh ganin har pass 12 Saleem bai Shigo gida ba,yasa kuma hankalinta yakara tashi tayi Safa da marwan Tsakanin upstair da kuma kasa,haka tazauna afalo tayi Zuru ta Tsurama kofar falo ido,lokacin da 12:30 tabuga ne Goggo Hadiza ta sauko daga sama tana bin Malika da kallon mamaki,itako hankalinta yayi gaba bata ma san goggon ta sauko sai da taji tana Fadin"Malika..."Cike da mamaki... Afirgice Malika ta Waigo ganin Goggo Hadiza yasa ta sauke ajiyar Zuciya tana Sosa kanta tace"Bakomai Goggo Zan kalli wani Shiri ne a Mbc yanzu..."Kallon mamaki goggo Hadiza ta Bita dashi tana karantarta kafin tace"Kuma shine kallon atsakar dare malika ..?Kina da danyen jiki,maza ki Wuce daki ki kwanta,dama na Shiga dakinki na kai miki su Aryan ne,sun yi barci kada Su tashi cikin dare suna kuka kinsansu da tsotso.."Kai ta sunkuyar Kafin ta Wuce tana Fadin"Toh Goggo sai da Safe.."Tafada jikinta asanyaye kafin ta haura sama da kallon Tsausayi goggo Hadiza ta bita kafin ta jinjina kai tabi bayanta,ammh tasan Dalilin wannan damuwar ta Malika,ita batajin Shigowar megidan ba Allah yasa lafiya. Koda ta koma daki kasa barci tayi wayarta ta Dauka ta latso mai kiran Daidai lokacin dayake zuba hon akofar makeken gidan, nashi megadi yataso ya budemai yana mai Barka da Zuwa shima cike da mamakin yau yallabai yayi dare,duk mai irin aiki irin nashi kowani lokaci zasu iya Fita. Sai da ya Daidaita motar a parking space kana ya daga kiran Malika wanda na Uku kenan ya Shigo wayarsa,Tana jin ya daga ta Fashemai da kuka Dan ware ido yayi yana Fitowa daga motar yake Fadin"Meya Abun kuka kuma..? Hmm mata sai abarku ku bata mutum rai kuma ku Fishi nuna ku aka cuta ko..?"Tana Share hanci tace"Don Allah Mallam ka ya Femin,ka dawo gida hakanan Hankalina yaki kwanciya Zuciyata tana Ta Tunanin kila ko kana tare da Wata ne.."Mirmishin gefen baki ya saki kafin yace"Na shigo gida yanzu.."Daga haka kawai ya yanke kiran,jin yace ya Shigo gida yasa ta Fito daga daki da sauri tana kallonshi ya Shigo yana Takunsa cikin isa,har ya hauro saman yana kallonta bai mata mgana ya Bude dakinsa ya Shiga ya maida kofa ya Rufe Ajiyar Zuciya Malika ta sauke kafin ta koma daki tana Share kwallar Daya Tarun mata. ******************* Har washegari Saleem bai saki ba,,sboda yana Fushi da ita ko karyawa baiyi ba,da goggo Hadiza ta matsamai ya tsaya ya karya sai yace zai karya a office in yaje,kuma Malika na zaune adakin goggon Hadizan daya  shigo gaisheta da Safe,Ayda kadai ya daga Data rugo tana gaisheshi ko su Aryan dake hannunta bai karba ba Daga hannunta ya lakace musu hanci yana musu wasa koda Malikar ta gaisheshi dakyar ya amsa kamar yana Ciwon baki ganin haka yasa Malika taja bakinta ta Tsuke ya har Fice,goggo Hadiza ba macece bace mai Shiga Sha"anin yara,kuma Abu na ma'aurata Shiyasa tayi musu bakam kamar bata Fahimci basu jituwa ba. Tafi tafi Fushin Saleem yama Malika tsauri wajen Sati daya Abu yaki Wucewa awajensa,gashi yanzu baya zaman gida kwata kwata,baya Shigowa sai around 10 kuma yana Shigowa zai Shige dakinsa ya Kulle,malika tanemi hanyar Sulhu ammh yaki bata dama,shiyasa itama ta Kama kanta,iyakarta dashi gaisuwa sai ko in ya Shigo dubasu Aryan,wani lokacin ma Dakin goggo Hadiza yake tarar dasu,ganin yadda yaki Fahimtarta shiyasa Itama Ranta ya baci da wannan Fushin mara Dalilin da Saleem ya Dauka da ita gabadayansu suka Share juna kowa na ganin Shi ba'a mai Daidai ba.   ****************** Ranar da Malika tayi Arba"in Ranar Ya marwan ya kawo joda gida domin cikinta ya Shiga wata na tara,kuma bashi da wani Hutu,shiyasa ya dawo da ita gida ta Haihu tunda chan kudu ne,koda hajiya ta kira Malika ta sanar da ita cewa kawai tayi zata kira jodan don yanzu bazata ce zata zo ba,kada ta kara wani laifin,Kuma shi Saleem din Ya dauko su daga Airport, Daganan Motar haya Ya marwan ya Shiga ya tafi Abuja achan ya kwana sai Washegari ya hau jirgi ya koma birin ikko don Ba"a bashi Hutu ba wannan ma Excuse ya dauka da zai kawo Joda gida. Har Joda tayi Sati da Zuwa ammh kuma Malika bata jeba,Bai cemata ci kanki ba,itama bata tayaba ta rabu dashi,Aranar kuma Yasa ka Direba ya maida goggo Hadiza gida,domin ta matsa zata tafi,saleem ya hadamata Sha tara na arziki hakama Malika tayi ta godiya tana saka musu albarka,Malika ko sai tayi kwallar harta Fadin in goggo Hadiza tatafi zata kara zama marainiya bata da mai kula da ita,itako goggon Hadiza tace Kina dashi mana Malika ga mijinki nan,Cewar datayi haka sai da Malika ta kalli saleem Shiko ya Hade rai kamar bai taba Dariya ba,sai da suka raka goggo Hadiza bakin mota dama Direban gidan Hajiya ne zai kaita,har suka Fice Daga gidan suna daga musu hannu,Shi Saleem yana dauke da Ayda ne,ita kuma Malika Ayyan ne ke Hannunta Aryan ya gama Rigima ya kwanta,Gaba yayi ya barta ita kuma tana Shigowa ta haura sama,Bai Shigo ba sai da Ayda ta tafi wajen su Merry shikuma ya hauro sama dakin Malika ya tarar da ita tana bama Ayyan Nono,Tunda taga ya Shigo Fuskarshi ba Fara"a tace topha,aiko illai gabanta ya tsaya yana Fadin"Miye Dalinlinki na cema goggo Hadiza in tatafi Zaki kara zama marainiya,wannan wata irin mgana ce,sai kisa tayi tunanin ko ina cutar dake ne fa.."Yafada yana mata wani kallo,kanta ta dago tana kallonshi idanuwanta sun ciko da kwallah,,ido cikin ido suke kallon Juna kafin ita tafara Janye idonta Hawaye Datake kokarin Rikewa suka zubomata tasa hannu ta Share Abunda ta iya cewa kawai Shine"Kayi Hakuri.." Yadda tayi ne jikinsa sai yayi Sanyi,duk Fushinsa sai ya sauka sausauta murya yayi yana Fadin"Kidaina irin haka ba dadi sai ta dauka wani abu ne.."Kanta na kasa ta dago tana kallonshi tace"Ba karya nayi ba,yanzu kadaina kula dani,Haba mallam takan laifin da nayi bisa kuskure kadan sai ka dauki Fushi dani mai tsawo haka,Sai yanzu nakeji ni Marainiya ce ada,ina ganin ka lullubemin maraicina amhhh.."TaKasa karisawa tayi Kuka taci karfinta da hanzari ya isa gareta ya zauna kusa da ita Ayyan ya karba ya Fita dashi sai gashi ya dawo Shikadai,Hannu ya mikata mata ta karba ya mikar da ita tsaye Habarta ya tallafa yana kallon kwanya idanuwanta kafin yace"waya gaya miki ke Marainiyace,Haba Amanata indai ina raye har abada baki ba kukan maraici.."Yafada Cike da kulawa,Runtse ido tayi hawaye suka kwaranyo mata kafin tace"Ka chanza mallam,ka barni inata wahala da Fushinka.."Harshensa ya sa yana lashe hawayenta,sai da ya lashe kaf,kafin ya Rumgumeta kam yana sakin ajiyar zuciya yake Fadin"Am srry Nayi kuskure insha Allahu baran kara ba.."Yafada yana kamkameta,ajiyar zuciya ta sauke tana zagaye kugunshi da hannuwanta,cikin muryan Sanyi tace"Nayi kewarka Abbu Ayda.."Ta fada tana sakarmai kiss Awuya kamkameta yayi yana Shinshinar Wuyanta kafin lokaci kadan sungama Rikita juna da salon wasanninsu,Cikin Fitan hayyaci suka raba junansu da kayan jikinsu,Kafin su Dangana da kan makeken gadonsu suna Tsotsan juna cike da kwarewa da muradi mai girma. Ranar dai ma"auratan komai ya Daidaita tsakaninsu Haka suka kwana manne da juna,don ma Rigimar su Ayyan ta hanasu sakat,ammh duk da haka Sun mori juna ba laifi Saleem ya Famshe kwanakinsa,dama gashi goggo Hadiza ta gyare yarta Sosai Acp ya yaba kuma yayi ta sambatu😂 ***********. Washegari kuma suka tashi da Lbrin Haihuwar Joda wacce ta haihu lafiya kalau agida,sai da safe Hajiya ta kaita Federal medical Center Katsina,aka duba ita Bby lafiyanta Kalau,Ta haifi da Namiji masha Allah,Dama Malika Ranar take Shirin zuwa sai aka tafi da murna gabadaya,Saleem ya ijiyeta agidan bayan ya Shiga yayi barka Shima ya Wuce office yabar Malika nan sai dare yazo ya dauketa,suna hanyar komawa gida yake sanar da malika zata fara hawa daya daga cikin motocinta da kanta,ammh sai dai su bari Weeked ya dinga koyamata mota,Malika tayi ta murna harda kwallar Farinciki,Abun yayi ma Saleem dadi ganin Walwalar Malikarsa zata dawo,domin shi yanzu babban Farincikinsa yaga Malika na cikin Farinciki akoda yaushe.. *Don Allah zan Rokeku wata alfarma Kada ku Cutar dani wajen Hadamin Malika waje daya bayan na kamallashi, na ganshi yana yawo agroups,kamar yadda ni Janafty nafada ba yadda zan mallaka ma mutum malika a 200 kachal,haba na be joking aie,kudin karatu kuka biya bana Mallaka ba,so plz and plz Kada ku Fitarmin dashi ko bayan nagama Don Allah na Rokeku..*🙏👏 *SHAKIRA*😘 *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏 _Kada ki karanta inda baki biya ba,inda kina so kiyi karatu cikin salama ki biya kudin karatu akan 200kachal👌 ta wannan account Nombar 0552179550 *JAMILA UMAR* Gtb ,ko kuma katin Mtn ta wannan Nombar 09069067488,Aturo hoton kai tsaye,ta Nombar dana bada_ *39* .............""Har Zuwa Ranar Suna Kullum Malika sai taje gida,in Saleem zai Fita office Tare suke Fita ya sauketa shikuma ya Wuce,Daga Hajiyar har joda sunji dadin Haka sosai,Yan Malumfashi sunzo mota biyu,mota daya daga barayin Dangin Baban Joda,daya kuma Daga Family dinsu Hajiya,wato Baffanin Malika kenan,hakama yan kumo sunzo duba bby,Sun kuma zo da Abun arzikisu sukayi barka suka koma. Ummi ma tazo,Da kayan suna Niki niki da nata dana Abbi dana ya marwan Wanda dama joda tazo da duka kayan Suna na bukatan da suka siya na haihuwa,sai kuma ya Turama Ummi kudi ta kara mata,Abun fa masha Allah sai wanda ya gani Ya marwan yazo kwana daya yayi ya koma inda yayi ma yaro Huduba da *SALEEM* wato yama Acp takwara kenan jin wannan Suna yasa daga Saleem din har Malika sukayi bajinta ban girma Malika makullin mota sur tabama Joda Shiko Saleem Kudi ya bata 100k ita kuma Malika ta dora mata Nata darin akai making 200k,Joda Saboda murna sai da ta Rumgume Malika kamar ta mata kwallar saboda godiya,Hakama Hajiya tayi ta godiya,itako Malika tace don Allah su bari,miye amfanin uban Dukiyan datake dashi in har batayi ma nata ba. Saleema ma tazo Ranar suna ta kwana ita da malika sai washegari ta koma Abuja ta kwana kafin ta Wuce,Taro ya tashi lafiya sai Fatan Allah yara young Acp,wanda suke kira da Junior. Hajiya ce ke Kula da Maijego da danta cikin kwanciyar Hankali,Hakama Malika itama tana cigaba da kula da kanta da kuma Mijinta da kuma ya"yanta,hakama Shima Saleem yana iya Bakin kokarinshi na ganin ya Sauke dukkan Hakkin Malika da na ya"yanshi daya Rataya awuyanshi,game da Harkan kasuwancinta Shi Malika ta dora Amatsayin manajojin kamfafoninta,duk wani kudi da zai Shiga ko Ya fita,ko in wani Abu ya taso,sai dai in Abu ya gagareshi sai ya Fadama Malika ita kuma amtsayinta na wacce tasan kasuwanci sosai sai ta Fitar da mafita cikin Lokaci,Shiyasa Kasuwancinta da Kudinta suke kara hauhauwa. Mganar koyamata Mota kuwa ya cika alqawari Duk Ranar Asabar da lahadi suke Fita da la"asar yana koyamata mota dayake Malika akwai kwalkwalwa basuyi wata ba ta koyi mota sosai,har tana tuka kanta taje gidan Hajiya ko asibiti,ammh bata taba Tafiya mai Nisa ba,sai dai ko cikin gari in zata Fita. Joda kuma ta cigaba da jegonta cikin kwanciyar Hankali ayayinda Da hajiya ke kula da ita,bata koma ba sai tayi wajen wata biyu,taje Abuja ta kwana biyu taje malumfashi ta kwana biyu Shima,har wajen Malika tazo ta kwana,Washegari mijinta yazo ya dauketa suka je Abuja suka kara kwana daya suka daga zuwa birinin na ikko da su da Little Acp dinsu wanda yayi kiba sosai yasamu Nonon uwa mai kyau da kuma kulawa in ka ganshi gwanin ban" sha'awa. Saleem ya saka Ayda awata private,sch Bby clss,saboda bakinta ya bude sosai ga Shigen wayau shiyasa Saleem ya sata amkaranta bakinta yakara bude achan,Malika ke kaita watarana taje ta ta Dauko Watarana kuma Saleem ya kaita kafin ya Wuce office in ko ya makara sai ya barta Malika ta kaita,Abun nasu cikin kwanciyar Hankali gefe daya kuma tana cigaba da Renon yan biyun ta suma da suka habake sukayi kiba sosai sai da wannan karon goyon Rigimammu take,don su Aryan akwai Rigima da daya ya Fara kuka,toh Daya zai dauka,Haka take Fama,don ma su merry suna kokarin Taimakamata da Renonsu wani lokacin. ******************* Zahra ta yi sanyi Fiye da yadda kuke Tunani ta chanza daga zahra ada ta koma Fatimatulzahra'u Wacce take da Tarin natsuwa da hankali yanzu ba wannam rawan kan,da kuma shigen iyayi bashi,Game da zafin kishinta kuwa ta Fahimci Halittanta ne,sai ta koma tana Rokon Allah ya rage mata wannan Zafin kishin,kuma Alhamdullah,Yamzu Abun ya fara ragewa ba kamar da ba.   Auren Nadira shiya kara maidata wani so silent,ada ta saba komai tare suke koda suka rabu da Saleem,kewar batamata yawa saboda Tana ganin Nadira ko banza zasu kwana tare su tashi tare,toh yanzu Nadira tayi Aure tana gidan Mijinta tana zaune lafiyanta,Ta kwantar da Hankalinta Da Zahra Taje gidan tayi mamakin ganin kibar da Nadira ta narka ya"yan Mijinta kuma shashenta suke Wuni Suna Anty kaza zanci ita kuma tana ta Ina kasa dasu,shiyasa ta Shiga ran iyayen kunsan me da wawa,Kwata kwata suna tafiyar da kishinsu Cikin tsafta Domin kunsan ba inda ba"a kishi sai dai akwai masu na ilimi dana Jahilci,Zahra bata fahimci Nadira nada ciki ba sai da ta sanar da ita da kanta tace mata tana ciki na tsawon wata Hudu,Abun ya daki zahra haka ta koma gida ta kulle kanta adaki tana kuka,Tana kara Nadamar Abunda ta aikata da"ace ta kwantar da Hankalinta da yanzu kila ta haihu Bama daya ba,ammh gashi har Nadira tayi aure jiya jiya har ta samu ciki,haka dai ta kwana kuka ta kuma yi alqawarin maida al"amarinta ga Allah ko zai kawo mata mafita. Momi tana iya bakin kokarinta wajen ganin Zahra ta saki ranta ammh sai ahankali Shiyasa ta Shirya musu Tafiya lagos wajen Hajiya baraka mahaifiyar Su Nadira,Zahra taji dadi sosai Balle ma hajiya baraka macece mai Fara"a da barkwanci Shiyasa Zahra ke jin dadin zama da ita,sati daya Momi tayi ta baro Zahra chan ta dawo kuma ba laifi zahra ta saki ranta dayake ta sake aure bayan Rasuwar Mahaifinsu Nadira,har ta haihu,Zaman lagos yayima Zahra dadi sai tayi wata biyu kana ta Biyo ya Nadir suka dawo tare wanda Suka isketa achan Shida matarshi Sati daya sukayi da zasu dawo da taboyosu. Bayan dawowarsu ne Ya Nadir yazo har gida ya samu momi ta complain Din zaman da Zahra take haka babu Abunda takeyi,gashi yaga Duk ta rame ta koma kamar Zahra bukar Mada,momi tayi bayanai ta yi iya bakin kokarinta ammh Zahra sai ahankali ganin haka yasa yasamu Abba ya mai mgana zai Nema ma Zahra aiki saboda zaman kadaichin yayi yawa,Bai yi mai musa ba,shiyasa ya karbi Takardunta bata da masaniyar komai sai da gidan Redion Freedom kano suka kirata interview Shi da kanshi yazo ya dauketa ya kaita tayi interview,cikin Nasara ko sati batayi da zuwa suka Turo mata sakon Sun Dauketa aiki ashashen labru,murna wajen Zahra ba"a mgana Haka ta Rumgume ya Nadir tana murna momi da Abba suna dariyan Farinciki Domin rabonsu da ganin murnan Zahra haka Har sun Manta Arana. Ranar data Fara Zuwa aiki Ranar Ya Nadir ya bata key din sabuwar motar daya Siya mata 4matic,mai kyau,Zahra kamar bakinta zai Tsage saboda godiya,hakama su Abba da momi suna mai godiya ya bata rai yace Haba Zahra fa yar"uwanshi ce saboda haka zai iya komai domin ganin Rayuwarta ta dawo kamar da,Haka ko akayi acikin Sabuwar motarta tafara Zuwa aiki Ranar,Data tashi kuma ta biya gidan Nadira ta nuna mata Sabuwar motarta itama Nadira tayi murna haka suka Rinka Dane motan suna Santi,ita kanta Nadira murna ya kamata ganin Zahra Ta chanza kamar ba ita komai yanzu tana yinshi cikin aji ne,ganin Zahra ta Shirya zata tafi tace mata zata biya gidan Ya Nadir,aiko Nadira tace sai taje Dr ta kira awaya tace mai zata gidan Ya Nadir ita da Zahra yace adawo lafiya,saboda kwakwa Nadira ita tayi Driving dinsu zuwa gidan ya Nadir suka kuma yi sa"a suka iskeshi agida nan Nadira ta sakamai kukan wlh itama sai ya Siyamata mota,Yako yace bazai siya mata ba taje mijinta ya Siya mata nan ta bare baki tana kukan Shagwaba Zahra da matarshi wacce suke kira Madam suna mata Dariya sai yammah Zahra ta maidota gida suna tafe suna Hira Nadira na kara Yima Zahra Nasiha da kuma hakuri da Rayuwa Zahra ta mata alqawarin insha Allahu ta chanza ita yanzu ko me mata Uku ce itace ta Hudu yazo ciki zatayi dashi ta gaji da zaman gida,Don ma dan aikin nan da Ya Nadir ya samo mata shike Debemata kewa ammh Kadaichin yayi mata yawa Sosai,Dama haka Rayuwa take Duk wanda baiyi Sharar masallaci ba to ai zai yi na kasuwa kodon Dolensa don Ubanshi.." ****************** Dalilin wannan Abun yasa Shakuwa tare da Tsantsan Damuwa da juna ta Shiga tsakanin Nadir da Zahra,shi duk a kokarinsa na ganin ta dawo Normal zahran ta kuma Alhamdulillah yabada Gudumuwaa domin ko Zahra bata dawo duka ba,tafara dawowa sai dai yanzu wannan Zahra ta gama Daukan Darasin Rayuwa sosai kuma ta kara gogewa da wayewa ba kamar da da bata wayau sosai ba,yanzu Saboda Cudanya da jama"a yasa idonta ya bude Sosai ta kuma gane Rayuwa. Wannan Shakuwarsu nasu ita iyayensu ke kallo da makusantansu suke zaton suna soyayye ne,kuma ba Haka bane,Kawai kulawa ne da kuma Shakuwa,hatta Matarshi ta Fara Shaka da Zahra shiko ko ajikinsa bai maida kai ba,hatta Nadira tana ta addu"an Allah sa Ya Nadir ya auri Zahra da tafi kowa murna Har Ummah su ta kita ta tsegumta mata itama Tayi murna Sosai bata kuma jira komai ta kira Abban Zahra ta sanar dashi wanda yaji mganar abazata Duk da dai Shima yana ganin Shakuwarsu ammh ko da ya tambayi momi sai tace batajin akwai wani Abu atsakaninsu,Ammh jin Batun Umman lagos yasa yace zai Nemi Shi Nadir yaji.. Koda ya kira Nadir ya zaunar dashi yana Tambayanshi shi ya kira Umman lagos yace yana Son Zahra,mamaki ya kama ya Nadir yayi Shuru yana hasaahen Daga ina wannan mgnar ta Fito ganin yadda yayi ne sai Abba yace kada ya damu in ba haka mganar take ya sanar dashi,girman Abba a idonshi da kuma Kimarsa da Yadda yake arayuwarsa yasa yakasa masa musu ya amsa da eh shi ya kirata ya sanar da ita,jin haka yasa Momi da Abba sukaji dadi sosai har suka kasa boye murnansu Afili,Shiko Ya Nadir zahra ya kira ya Fara tambayanta itama taji mganar tayi mata bazata Tace itama bata sani ba,sai da ya kira Umman lagos yake tambayanta ta kyalkyacemai da Dariya tana gayamai yadda sukayi da Nadira tace taga ya tsaya kunya Shiyasa ita ta kira baban nashi ta sanar dashi kada wani yamai Shigar Sauri,ganin yadda gabadaya lamarin ya Daure Nadir shiyasa ya share bai nuna ma kowa bai ta ma Zahra kallon Wacce zai ya Aura ba yana kallonta ne da Sigar dayake kallon Nadira,ammh kuma Abba ya Wuce haka agurinsa bazai taba watsamai akasa a ido ba,Zai auri Zahra koda baya sonta ai kanwa take awajensa.. Tunda Abun na gida ne Umman lagos ne kadai tazo aka sanya Rana wata biyu masu Zuwa sai lokacin Ya Nadir ya sanar da matarshi,Taji wani iri sosai kuma bata iya boye kishinta ba,harta koken ko don bata taba Haihuwa ba yasa zai kara aure,lallashinta ya shiga yi da bata bKi har ta sauko ta karbi mganar hannu bibbiyu ta kuma yi mai Fatan alheri Duk da kishin Mijinta na cinta ammh ta danne Tunda dai mijinta bai Chanza mata Daga Son daya ke mata,Sai dai Wani dan Abunda ba",a raasa ba Tunda Dan adama ajizi ne Tara yake bai cika goma ba. Zahra ma haka taji Abun kawai Daga sama,Ammh kuma akasan Ranta tayi murna Domin Shima ya Nadir Namiji ne,Kodai baikai Saleem ba to zata jerasu a Aji da Takama da isa,lokacin daya Fara zuwa wajenta da Sigar Mijin da zata aura yayi mata mganganu sosai ya kuma sanar da ita sai tayi Hakuri don yana mata kuma ta sani,so suyi Hakuri da juna duka sai su zauna lafiya,Zahra bata daukan ma kanta Tun Farko ba,tuni ta watsar da wani kishin Banza ta rike Sabon Mijinta kuma yayanta dakyau gefe daya kuma suna ta Shiryen Shiryen bikinsu,da farko ita fara wasan buya da Madam,sai da bita har wajen aikinta bayan ta dawo daga asibiti tana mata tsiyan haka zasu kwashe In ta Shigo ai an zama daya,Zahra tayi murna sosai nan da nan suka koma kamar da,wani lokacin in Zahra tatashi Daga wajen aiki ta kan biya,Nadira kuma ta fikowa murna kamar me,tana ta addu"a Allah yasa kada ta Haihu sai bayan biki cos tana son ta baza kara"i ne part 2 awannan karon. Biki ya karato Duk da ba gayyah Zahra tayi sai yan wajen aikinsu kawai sai wasu daga cikin kawayensu da sukayi mkranta Zahra ce ta matsamata ta kira Saleema ta Sanar da ita zatayi aure,bata yi musu ta karbi lambarta ta kirata sai da ta sanar da ita Sunanta kana ta ganeta Saleema tayi mamaki sosai kuma tayi murna da jin Zahra zatayi aure,nan take Sanar da ita Tayi Nauyi ammh zata Roke Ya Sadiq in ya yarda zata zo Katsina ta kwana sai su taho tare da Malika,jin haka yasa Zahra tace ta Rubuto mata Full address din gidan Saleem da lambar wayar Malika nan ko take Saleema ta tura musu suka rabu cike da Farinciki kowa na Mamakin yadda dan"uwansa ya chanza wai Saleema keda ciki wai Chanchadi😂 Nadira tabama Zahra Shawaran taje Har katsina ta kaima Malika Katin biki da cimgam,da kuma nemam ya Fiyan juna Tunda yanzu komai ya Wuce,Zahra ta yarda da mganar Nadira hakama momi ta amince mata taje,domin itama tace zata kira Ummi ta sanar da ita Ranar bikin,Nadira ta so ta raka Zahra ammh sai Dr ya hana Don cikinta ya tsufa,Shiyasa Ana saura kwana goma biki Zahra ta Tafi katsina da kanta ta tuka kanta cikin Sabuwar motarta ammh sai da ta tambayi ya Nadir ya kuma bata dama. _Insha Allahu *MALIKA MALIK* Zai kare a page 40 ne,Duk da ba haka na so buh Lbrin ne yazo ahaka,Darasin ya Fita,kun ilimantu kun Nishadantu da abubuwan dake ciki bayan Tarin Fadakan da kukayi,ina Fatan zakuyi amfani da Abunda kuka ci karo dashi mai kyau zaku watsar dana Banza...Babu amfanin tsawaita lbri tare da Jan rai matukar an cimma Abunda Ake Nema,Allah kabamu ladan Taruwa dani da ku wajen Wannan Rubutun..._ *SHAKIRA* *JANAFTY* *ANITHA* *MOMYN LADINGO* *MALIKA MALIK...!* _(Sai na rama..)_ *_Mallakar:Janafty_😘* *KUDUBI GIRMAN ALLAH KUREMIN AMANATA,NAYI MUKU ADALCI NIMA INA BUKATAR KIYIMA KANKU KUYIMIN ADALCI KADA KU FITARMIN DA BUK WAJE DON ALLAH*🙏               *KAR'SHE...*👏😰🙌   ....."Full Address Din da Saleema ta Turo mata tabi da kuma tambaya sai gata abakin makeken get din gidansu Malika tana zuba hon da hanzari megadi yazo ya wangale mata get yana mata barka da Zuwa,yana zaton kawar Hajiya Malika ce. Aparking space ta adana motarta kafin ta Fito tana Sanye da abaya doguwar riga baka ta kamfanin Armani Wacce ta yane kanta da karamin bakin gyalenshi, Kafarta Sanye da Cover baki,mai wani Fulawan baki Ajikinsa,sai karamar bakar jakarta dake hannunta Hade da key din motarta cikin Sha"awa take bin gidan da kallo kafin tafara taku Zuwa Wata kofar glass din da zai sadata da cikin Babban Falon gidan. Tana sa kanta Falon Cikin Sallama Da karamar muryanta kamar ba Zahra ba, babu kowa a makeken Falon,sai karar Talabijin din da ta kusa cinye bangon Wajen Saboda Girma,tana kokarin sake Maimaita Sallaman nata ne Sai ga Merry ta Fito dauke da Aryan ahannunta yayinda Dose ke Tura Ayyan a wani karamin keke da alamun na koyon Zama ne... Da kallo Zahra ta Bisu dashi tana Mamakin Yaushe Malika ta Sake Haihuwa Domin ko ba"a Fada wannan ya"yan Malika ne da Saleem Saboda yadda suka kwaso kamanin Babansu da kuma Hasken Fatan Mamansu,Merry ce Tafara gane Zahra cikin Mamaki da doki ta Furta.."Anty...."Tafada cike da mamaki da Murna lokaci daya. Mirmishi mai Sauti Zahra ta Saki kafin tace"Yes Merry.."Tafada tana mika hannu ta karbi Aryan daga hannunta tana Fadin"Ina Malika..? Ko bata nan ne..? Dose ta gaisheta ta amsa cikin sakin Fuska tana ma Ayyan wasa hannunta na dauke da Aryan,Da hanzari merry ta Haura sama ta kwankwasa dakin Malika,wacce Fitowarta wanka kenan tagama Shiryawa kenan cikin wata Atamfanta Riga da Sikat,tana Daura Dankwali tazo ta bude kofar ganin Merry yasa tace"Merry anthing..? Merry na Washe baki Tace"Anty Zahra ce tazo tana Falon kasa tana jiranki.."Cike da Mamaki Malika ta Furta"Wata Anty Zahra..", Merry tace"Wacce kuka zauna atare Azamfara Anty.."Cike da Mamaki Malika ta zaro ido tana Fadin"Zahra..!Sure.."Merry tana Dariya tace"Very Sure Anty.."Malika bata jira Cewar Merry ba Fito daga dakin ta Sauko kasa merry tabi bayanta cikin Sarsssafa Malika ke saukowa daga Steps idanuwanta na cikin na Zahra tana Saukowa ta karisa gareta tana Fadin"A"a Hajiya Zahra ce yau agidan Namu..? Tafada tana sakin mata murmishi lokaci daya kuma ta bata hannu suka Sarke cike da Farinciki Zahra tace"Wlh kuwa,Na sameku lafiya ya yara,ina Ayda nasan yanzu anzama yan Mata..? Tafada cike da kulawa,Dariya Malika tayi tana Fadin"Lafiya lau wlh,yara gasunan,Ayda kuma tana mkranta basu taso ba.."Tafada ta karisawa da Zahra bisa daya daga cikin kujerun Falon suka Zauna Zahra na Rike da Aryan,da hannu tama Dose alamun ta miko mata ayyan Duka ta Hadasu ta rike Tana Fadin"Masha Allah yan Biyu kyautar Allah.."Take Fada tana musu Wasa,Malika kuma ta umarci Merry data kawoma Zahra ruwa da Lemo nan da nan ko ta Shako mata Faranti guda da lemuka da Ruwa tazo taja karamin Center Table din dake Tsakar Falon ta ijiye akai kafin ta Zuba ma Zahra Ruwa ta mikamata ta karba tana Fadin"Tanque Merry.. Sai da tasha Ruwa kana suka kara gaisawa da Malika cikin Fara"a tare da Tambayan Yaushe gamo,malika ta Tambayi Nadira,Zahra tace da tare zasu zo,Ammh Mijinta ya hana Saboda tayi Nauyi baki malika ta rike tana Dariya take Fadin Allah ya Raba lafiya Kwata kwata Malika batama Zahra bakunta ba ko ta Nuna mata wani abu ba,Ta saki jikinta Sosai tana ta janta da Hira tana tambayan mutanen gidan,Cikin hiransu ne Zahra ta Fitoma da Malika katin bikinta ta Bata tare da Sanar da ita tana gayyyatanta,cike da Farinciki Malika tace insha Allahu zata zo indai Saleem ya barta,Shuru Zahra tayi kafin ta Sulale kasa tana Rokon Zahra gafara bisa Abunda ta aikata gareta Rikota Malika tayi tana Fadin"Wlh banta ba Rikeki ba Zahra,Da ina da yarda zanyi da Tuni Mallam ya dawo dake dakinki mun zauna tare,Ammh bani da yarda zanyi,har ga Allah Zahra banta rike ki ba har azuciyata ba.."Zahra na Sharan kwallah takema Malika godiya bata jima tace Zata tafi Malika ta Hanata tace ta bari ta kira Mallam yazo su gaisa,Ita kuma taki tace tafiya zatayi bataso tayi Dare ahanya,suna cikin mganar ne sai ga Saleem ya Shigo Shida da Ayda yana office ya samu wayar Shugaban mkrantan su Ayda an tashesu tun dazu ammh har yara sun gama watsewa Ba"a zo an dauki Ayda ba kuma yayi ta kiran Wayar Malika bata daga ba itako Zuwan Zahra ne ya Mantar da ita komai,kuma wayarta ta barota asama... Shima yayi mamakin ganin Zahra,ammh sai ya Shanye mamakin ta hanyar Hade ransa itama Zahra gabanta na Faduwa ta duka tana Gaisheshi adakile ya amsa yana Shirin Haurawa sama Malika tace"Mallam zahra fa gayyatanmu tazo yi zatayi aure upper week insha Allahu..'Bai waigo ba yace"Allah ya sanya alheri.."Daga haka ya Haye sama ya Shige dakinsa ko waigo,duk da Malika bataji dadi ba,ammh Sanin Halin gogan nata sai ta barsa,itama Zahra haka taji ammh sai ta Share ta bar Abun duk laifinta ne,kuma bata ga laifinshi ba,don ta chanchanci Fiye da Haka... Girman Ayda ne da wayonta ya bata Mamaki haka ta dauketa tana Tambayanta Sunanta tace"My Name is Fatima Saleem kabir kumo,know as Ayda.."Baki Zahra ta rike tana mamakin Ayda Malika na musu Dariya domin Ayda akwai kwanya kuma dayake wani lokacin Duka iyayenta basu mata mgana da Harshen Hausa sai dai Turanci gasu Merry ma basu mata mgana da Hausa Sosai dat why tatashi dashi abakinta koda ta Shiga mkranta Abun bai bata Wahala sosai ba. Zahra bata tafi ba Sai da Malika ta matsamata ta ci abinci kana ta rakota har Wajen mota suka rabu bayan Malika ta karbi Digit din Zahra da alqawarin insha Allahu zata lallaba Mallam zata bikinta da Yardan Allah,Zahran Tadai jita je,ammh ganin Yadda Saleem din yayi batayi tsammanin Zai Barta tazo ba,da zata tafi tabama Ayda 5k ita dasu Ayyan bayan Tarin tsaraban data zo musu dashi na Chaculate,suka rabu cike da kewa har motar Zahra ta bar Haraban gidan Malika da Ayda da su Merry suna Daga mata hannu. Koda Malika ta dawo cikin gida Saleem bai mata mganar Zahra ba itama Sai ta Share bata Tankashi ba har Washegari kanzil bai Ce mata ba,kuma yana ganin Ayda ta saka Rigima da safe ita sai an saka mata chaculate din da Anty Zahra ta kawo mata cikin basket dinta,Yana jinta tana Fada da ita kan Shan zaki,sai ma tasowa yayi da kanshi ya kwashi Chaculate din ya Zuba mata cikin jakarta ya kama hannunta Suka Fice daga Dakin,da kallo Ta bishi kafin Ta murmusa,domin inda sabo ta Saba da Halin Miskilamcin Saleem. Har Bikin Zahra Ya matso Saleem bai cema Malika komai ba,Ana jibi bikin Saleema ta kirata awaya, tana Tambayanta in zataje Zata zo gobe sai su Wuce Kanon Tare,Malika bata yanke mgana ba Sai da Saleem ya dawo da daddare take Tambayanshi Zuwa bikin bai ce mata komai ba,balle ta saka Ran Zuwa har Washegari Ta kira Saleema tace bazata samu Zuwa ba,Suka Rabu da Saleema kan zata Abuja aranar jirgi zata biyo gobe Direba zai kaita Kanon Tunda dai Tayi Ra"ayin Zuwa. Sai da Daddare har sun kwanta yace gobe ta Shirya Zasu tafi Abuja gabadayansu Suyi Hutun karshen Mako daganan sai tabi Saleema su Tafi bikin Murna ta kama Malika har Sai da tayi tsalle ta Rumgumeshi tana Murna,gari na wayewa,koda 11 tayi tayi musu Abuja dama already ta kira Saleema tace ta jirata gatanan Zuwa tana Zuwa basu tsaya Ba,Direba ya kwashesu Zuwa kano,Ayda ne ta tsaya wajen Ummi da Babanta,Merry kadai Malika tataho da ita,saboda Kula dasu Aryan,Dose kuma an barta Wajen Ummi. Koda Su Malika suka Isa gidan Su Zahra,Hatta da Momi tayi murnan ganinsu,balle ma Da Malika ta bata 50k Gudummuwar biki,tayi ta mata godiya  Sosai ballatana Zahra da Nadira Wadanda suka Rasa ina zasu sakasu saboda Murna da Farinciki kamar yadda Saleema ke Fama da ciki Haka Nadira ke Fama dashi Haihuwa yau ko gobe,Zahta tayi kyau Sosai in ka kalleta baka kirata bazawara ba,Saboda tana kyan jiki,kuma batataba Haihuwa ba,La"asar nayi aka kai amarya gidan Ya Nadir dake kusa da asibitin Murtala,tare ya Hadasu da matarsu,Zahra tasha Fada da Nasihan Hakuri da juriya,Zafin kishi kuwa Tunkafin wani yayi Mata Fada Duniya tayi mata,shiyasa yanzu taWatsar da komai ta kama Allah ta Shiga da Zuciya daya cike da alheri. . Su Malika basu samu dawowa Aranar ba sai washegari Saboda Dare yayi musu Gidan Nadira suka kwana,sai da Safe suka kamo hanyar Abuja bayan Sun Biya gidan,Zahra sun mata sallama suka Rabu cikin kararramawa da Farinciki,tare da alqawarin in Saleema ta Haihu zasu zo,suma sukace in Nadira ta sauka su Sanar dasu insha Allahu zasu zo. Ranar da suka dawo sai yammah Suka Shigo shiyasa Su Malika basu koma katsina aranar ba Sai Washegari suka Wuce da Safe ita kuma Saleema jirgin yammah Tabi ta koma Don taso Sadiq ya barta ta zauna Har ta haihu ya nuna bai yarda ba kamar ma ya nuna achan yakeso ta Haihu,Allah barshi sai aturo wacce zata zauna da ita,ammh Bashi da Ra"ayin Ta dawo gida wanka,Dole ta Hakura ta koma bayan Ummi ta bata bakin in Ta haihu ita zataje ta zauna mata,Hajiya tace gata itama zata Dole ne,jin haka shiyasa Saleema ta koma Cikin Farinciki. ____________________ *BAYAN SHEKARU GOMA DA SUKA GABATA* ....."Ashekarun goman da Suka Wuce Rayuwa ta gangara yadda Allah (SWA) ya tsara Abubuwa dadama na Farincikin da akasinsa Sun Fara acikin Rayuwar Saleem da Malika,Na akasin Farincikin Shine Shekaru biyar da suka Wuce Sukayi Rashin Hajiya Babba Wacce Ta Rigamu gidan gaskiya Sai Fatan Allah ya jikanta da Rahma,mutuwar Data girgiza Iyalan Kumo gabadaya Saboda yadda Hajiya Babba take awajensu,ammh kuma basu yarda zasuyi Mutuwa tana kan Kowa muma ita muke jira. Ababen Farincikin da suka Faru kuwa,Shine Shekaran daya Gabata  IG KABIR KUMO yayi Ritaya daga aikin yan Sanda,wannan Dalilin hakane bayan an samu chanjin gwannati aka Tsaga sunan SALEEM KABIR KUMO amtsayin IG Na kasa gabadaya,wanda Dama kafin lokacin yayi ya samu karin Girma yana mtsayin AIG ne. Rayuwa tayi kyau Fiye da Zaton mai karatu inda Zuru"a suka cika gidan Kabir kumo wanda Suke nan Zaune har yanzu agarin Abuja,Suko su Malika Sun baro katsina Suna Zaune a wani makeken gidan Da Saleem ya Siya Mai kama da aljannar Duniya,bayan Ayda da Ayyan Takara Haihuwan Mata biyu Maza biyu,Ya"yanta Bakwai kenan,inda take da Saleema da Marwan,sai Abubakar Da Maryama,Ayayinda itama Saleema take da ya"aya biyar Cif Duka mata,Hamdiya,Hamida,Hafsart,Hadiya,Aneesa,Ya marwan ma Tuni ya"ya Sun lullubeshi shi da Joda ,ammh sukan suna Tsara haihuwan ne,Ya'yansu Uku Saleem,sai Saleema,sai Fatima wacce suke kira Ummi kenan.Ayanzu haka Sunbar lagos sun Dawo partacourt da zama Sakamakon Chanjin wajen aiki da ya marwan ya samu hakama Sadiq suma yanzu su suka koma lagos da zama sakamakon Shima ya samu karin girma Zuwa DCG,Sun tattara sun koma chan,sai dai duk bayan Wata uku suna kokarin Zuwa Abuja Hutu domin Ganin iyayen nasu da kuma Sauran yan"uwa. Abbi Da Ummi sun Fara manyanta Duk da Kudi da Hutu Suna Boye manyantansu nasu,ammh sun Kara manyata Sosai Saboda Shekaru yaja,ita kanta Ummi tayi Ritaya daga aikin lauyan datake yi saboda Shekaru Sunja kuma Jiki yayi Nauyi,Ganin yanzu Ummi ta Manyanta Shiyasa Suka sama mata masu kyau har Biyu wadanda zasu rinka Taimakamata,Ya"yansu suna kula dasu sosai musamman ma Saleem da Malika Wadanda ke kusa dasu,Kafin Rasuwar Hajiya Sai da Sukaje kasa mai tsarki dukkansu,ahalin wanda Malika ta biya musu Dukkansu sukaje kasa mai Tsarki suka sauke Farali,ita ko da Saleem da ya"yansu basu san adadin Hajji da Umuransu ba,saboda sun mai dashi kamar zuwa Abuja daga Kano ne Hajiya Malika Wacce ke Amsa mtsayin Malika Abdulmalik Dankasuwa,ada Sunan Mahaifinta ne yake yawo Aduniya amtsayin Wanda ya Mallaki Dukiya mai yawa,ammh Zuwa wannan Lokacin Sunan Malika ne ke yawo a ko"ina Domin ta Samu Cigaban kasuwancinta Sosai,kuma da Taimakon Mijinta ta Maida hannayen Jarin Dukiyarta Zuwa kasashen ketare,Malika tayi kyau sosai Fiye da Tunanin mai karatu ta kera jiragen sama Sunfi guda goma,ta kire Jiragen kasa,suma ba adadi bayan Ta bude Wani kamfani a kasar America,na Kera motoci wanda da Farko hannu jari ta Hada dasu sai kuma Daga baya ta Siya wajen ya zama mallakinta,agida Nageria ta Budema Matasa Shaguna Kala kala domin Dogaro da kai,Riba kadai zaka bata awata sauran Kudin nakane,Malika ta abude Gidan Marayu agarin Malumfashi da kumo,wanda ke amsa Sunan *MALIKA ABDULMALIK ORPHANS* Bayan haka kuma ta na da Kungoyoyi na Taimakon al"ummah mussaman ma ya"ya mata marasa galihu expecially Kungiyarta na MALIKA MALIK FOUNDATION kungiyace data ke Taimakon Mata da kananan yara,wadanda basu da iyaye ko kuma iyayensu basu da karfin da zasu dau Dawainiyarsu ta bangaren karatu da Sauransu akallah ta Dauki Nauyin karatun yara mata da maza Wadanda batasan iyakarsu ba,ta Fita da wasu kasashen wajen wanda suma bata san iyakarsu ba,tana DA office akaduna da Abuja,Tana da ma"aikatan na kusa da ita kamar Joda da Su Saleema Harta su Nadira da Zahra bata barsu ba,ta basu Mikamai acikin wannan kungiyar nata Suna taimakamata da abubuwa dadama,in wani Abu yataso zasu kirata Su Tattauna,duk da yanzu Dukkansu sun zama manya mata domin Nadira ma ya"yanta Biyar,sai Zahra dake da Hudu aciki harda takwaran Malika,harta Saleem din yanzu ya yarda komai an Dawo ana zumunci an zama Daya. Malika bata Shiga Siyasa ba ammh an Sha kawo mata tayin haka,kawayenta yanzu sune Matan Manyan Sojiji,da matan Sarakuna kowani yanki tare da Matar Shugaban,kasa da Matan Ministoci Duk da su suke Shige mata ganinta Macece da bata da kyashi ko kadan,itako tasan zaman data take da kowa,Lbrinta Babu inda bai Tsaga ba ko"ina afalin Kasar Nageria da ketare ba gidan Tibi da jaridan da bata hira da ita,ba gidan Radion da bai gayyaceta yayi Hira da ita ba,duk kuma wannan Abun bai samu ba sai da goyon bayan gwarzonta kuma bangonta Mijinta Uban ya"yanta Wato *SALEEM KABIR KUMO* Domin Shi ya bata duk wata dama na yarda zata Gudanar da Rayuwarta ta Hanyar Taimakon mutane da Dukiyar da Allah y bata,duk inda aka gayyaceta wani taro baya haufin barinta Tunda zatayi Shiganta na Mutumci taje,ya"ya kuwa Ayda tana Wajen Saleema Domin Malika ta cika alkawari ta bata,Su Aryan kuma suna gidan su Ummi,sai su Maryam wacce Suke kira Hajiya da Abubakar Wanda Suke kira Sadiq,sai Saleema Ummita,sai Marwan da Suke kira Khalipa,Su kadai ne yanzu agida Agabanta suma din sun girma ba yara bane,sun iya kula da kansu musamman ma Ummita da Sadiq Tunda Sune manya,Mijinta kuma bata iya hadashi da kowa matukar Suna gida Dukkansu to kashe wayarta take,musamman ma Ranar Weeked dukkansu basu Fita ko"ina sai dai in Wani kiran gaggawa ne ya taso,suna Makale da juna suna kara jadaddama Juna irin son da kowanne yakema Dan"uwansa. Merry da Dose dukkansu sun Musulunta Merry ta koma maryam ita kuma Dose tace ita Sunan Madam take so Malika,ganin ko sun koma garinsu Danginsu Bazasu Amshesu ba yasa Saleem da Malika suke Rikesu tamkar ya"ya yanzu Haka dukkansu Sunyi Aure,ammh Maryam merry tana nan Tare dasu don mai kula da Gidan Gonar Saleem take Aure,suna zaune agida daya,wani lokacin in Duka iyayen basu nan,shashenta su Ummita ke Zuwa ta kula dasu har iyayen nasu Su dawo duk da Sun Dauko goggo Hadiza tana zaune dasu,in ma anyi Hutu kenan in ko Lokacin mkranta ne dukkansu Mkrantan kwana Sukeyi nan Nagerian Turkish acdmey,ita kuma Dose Malika tana kaduna tana Auren Wani Matashi suna daga cikin Wadanda Malika tabama Jari domin dogaro da kai. Malika ta Waiwayi Dangin Mahaifiyarta Dga Baya Tafiyar Datayi Shi Tare da rakiyar Mijinta Da Duka ya"yanta har Zuwa birin England,koda taje yawancin dangin Maman nata Duk Sun kare,saboda dama basu da yawa wanda suka rage kuma talauci da Taufa sun Rikitasu sosai,Dakyar ma wasu suka gane Malika Diyar Juliyat ne,suka Rumgumeta Suna kukan Murna,Malika tayi takaichi mai girma na yarda ta Fito daga wannan Tsatson ammh kuma bata da yarda zatayi wannan Shine zanen kadaddaranta,Sati daya sukayi kafin su dawo gida bayan ta cikasu da kudi Sosai da duk Abunda kowa Zai Bukata,kafin su taho da yawansu an samu Wadanda suka karbi Musulunci,Wasu anan ta barsu,wasu kuma ta taho dasu ta basu wajen Zama da aikin yi.Sai gashi Malika ta zama Abun alfaharin kowa,kowa na so yaji wani yace yana da alaqa da ita,kuma kowa na jin dama matar dana ne ko kuma dama kawar yata ce,saboda kyawawan Dabi"unta da kuma Yadda take kokarin Taimakon addininta da kuma Talakawanmu marasa karfi. **************** ""Yau din takama Weeked ne Ranar Sunday kenan,gashi suna cikin Hutu ne dagasu har yaran,Tun jiya da Daddare da suka dawo Daga kano,wajen Taron Na Malika malik Foundation inda ta gudanar da Bada Kudaden da za"a ma yara yanmata guda Hamsin kayan daki wadanda zasu aure ammh iyayensu basu da Hali sosai Shiyasa kwamitin kungiyar ta jahar kano Ta nemi data Taimakamusu,wannnan Shine Dalilin Zuwanta Kuma Alhamdulillah Ta taimaka Daidai gwargwardo,duk inda taje bata kwana Koman dare zata dawo,shima Saleem din bayanan ajiyan sunyi Taro Afadar Shugaban kasa,shima sai dare ya dawo Dukkansu Tunda suka kwanta sai barcin gajiya Dakyar suka iya tashi Sukayi sallar asuba suka koma suka kamkame juna suna cigaba da barcin gajiya. Ummita da Sadiq Tun daren Jiya suka Hada kayansu Tsaf sukace wannan Hutun Sufa gidan Goggo Saleema zasuyi shi,su kuma hajiya da Khalipa suka ce ada sunzo zuwa gidan Ummi ammh Tunda su Yaya aryan na chan sun Fasa,yanzu Gidan Dadddi zasu je su gama Hutunsu achan,tunkafin Ranar suka Shaidama iyayen nasu ammh sai sukace su bari Weeked sai su Tafi,ammh gashi Weeked tayi Dukkansu basu Wuni agida ba,ga yau ma tayi ammh dukkansu babu Wanda ya Sauko kasa. Tun Karfe 8 na Safe suka Shirya kowanne ya jayo Trolley dinsa ya kame kan Kujera suna Jiran saukowan Iyayen nasu,kowanne ya kurama upstair ido yaga ta ina zasu bullo,Da ka kalli Fuskarsu zasu tabbatar da Ransu bace yake,gashi Tarbiyan da iyayen suka basu babu ta Shiga musu dakin barci indai basu tashi ba,Baba Larai mai aiki wacce Suka daukota daga Kumo tayi tayi suzo su karya kowanne ya Tura baki yana Fadin"Am ok.."Dayake yaran Sun taso cikin Tarbiyan iyayensu suna da girmama na gaba dasu,sannan Saboda yadda bakinsu ya saba ko"ina sukaje ba kasafai suke mgana da Hausa ba,sunfi saka yaren Turanci abakinsu ta wani bangaren kuma suna jin larabci sosai saboda Abbansu ya iya Shiyake koya musu,balle kuma Malaminsu wanda ke koya musu karatu bayan sun Dawo Hutu Mallam Usman baya musu mgana cikin harshen Hausa Shiyasa suka iya,duk bangaren Daka tabosu basu da wasa. goggo Hadiza ta kalli Ummita tana Fadin"Ummita Wannan Hade Fuska kuma Duk tamana yaji ne..? Tura baki Ummita tayi tana Fadin"Goggo Hadiza ,Su Mommy fa sukaki Fitowa,Alhalin kuma mun Fada musu zamu Hutu yau gidan Goggo Saleema..."Sadiq ya karbe da Fadin"Eh wlh,kuma lagos ba kusa ba,Ni addu"ata Allah sa ko Daddy ne yafara Fitowa da Mommy kunsanta in tayi Tafiya ta gaji bata Fitowa da Wuri."Baki khalipa ya Tura kafin yace"Ni fa na gaji da zaman gidan Allah bai kawo Wani light."Yafada yana Cije baki Hajiya ce karamarsu yar Shekara Shida tace"Nidai ina son zama da Mommy da Daddy muyi ta hira.."Harara Ummita ta sakarmata tana Fadin"Ji wannan,Yasin ki ma kama kanki don Daddy bayason Hira da kowa sai Mommy su kule suki Fitowa mu su barmu da game ko kallo,gwara muje Hutunmu mu hade da Ya Ayda ehyyyyr..."Tafada tana Ihun murna,Goggo Hadiza da Baba larai na musu Dariya. Hajiya tace"Toh zan biku gidan Goggo Saleema.."atare Ummita da Sadiq suka taso suna Zaro ido lokaci daya suka ce"Ina....?,Waza ki bi..? lalle ma yarinyarnan kima kama kanki Tun Wuri don Wlh bazaki bimu ba,tabdijam ki Wuce kibi Khalipa gidan Daddi.."Jin haka yasa Hajiya ta bare baki ta saki Kuka harda buga kafa,Suko mai zasu yi banda Mata Dariya itako tana kukan Wlh sai ta bisu Gidan Goggo Saleema. Daga chan Sama Sukaji muryan Daddynsu yana Fadin"A"a Wa Yatabamin Hajiya da Safen Farin haka.?."Dukkansu suka Kurama inda sukaji muryan Daddynsu ido,Dan matashin Dattaji ne yana Sanye da Jallabiya Mai Ruwan Toka,Idanuwansa suna lullube da Farin glass mai kara karfin gani,Kallon Farko zakama Saleem lokaci daya zaka Fahimci yafara zama Dattijo,domin har Farin gashi yafara bayyana a kansa,duk da Halittace dan kimamin Shekaru 50 aduniya ne ayanzu Bai kara kiba ba,sai sai yakara Murjewa da Kuma kara haske Saboda Hutu da kuma karin Jin Dadi. Hannunsa na Sarke cikin na Malika Wacce ke Sanye da Wata abaya Doguwar Riga kirar Armani,Ta yane kanta da Wani jan Vail domin kwalliyan adon Kayan Red colour ne,Kyakywan Fuskarta wacce bata bayyana alamun Tsufa ta bayyana Sosai masu jere da Hakoran makka guda biyu,wanda suka karamata kyau,duk da Shekaru sun ja,ammh bazaka taba ganewa ba,saboda Hutu da jin dadi sun boye hakan sai dai zaka Fahimta da yanayinta Tunda ai jiya ba yau ba, Da gudu Hajiya ta ruga ta Rumgume iyayen nata dake kokarin Saukowa daga Steps,cikin hanzari Saleem ya Saki Hannun Malika ya Daga Hajiya Sama yana Fadin"Waya taba min ke..? gayamin yanzu na masa bulala..? Kwabe Fuska tayi tana kara Rufe ido Tace"Ba su Ya Ummita ba ne,da ya Sadiq bane suka ce bazasu dani gidan Goggo Saleema ba.."Tafada Tana kara Saka kuka,Dariya ta kama Malika tasa hannu ta karbi Hajiya suna karisawa saukowa daga Steps take Fadin"Wa ya isa..? Manta dasu ke kadai ma zaki Hutu wannan karon.."Tafada tana Dagama Ummita gira wanda suka kara Hade rai jin Abunda Momy tace. Goggo Hadiza sai dariya take Ganin yadda yaran suka kara Hade rai Suna kunkuni,suko iyayen nasu namusu Dariya ganin yadda sukayi ne yasa Hajiya dake hannun Malika ta hau ti musu gwalo,Zuciya ta Ciyo Ummita ta mike tana Hararanta,Saleem ne ya Daga mata hannu yana Fadin"Hy duk wannan Bata Fuska da Fushin na miye ne Ummitan Daddy..? Goggo Hadiza ce tace"Fushinku ne,nan fa duk jiran saukowanku Suke sun Shirya tsab yau sai Tafiya Hutu.."Sai lokacin suka Lura da manyan akwatun nasu dake Tsaye awajen Baki Saleem ya kama yana kallon Malika kafin su Gimtse dariyansu,Saleem ne ya zauna tsakanin Ummita da Sadiq ita kuma Malika ta zauna gefen Khalipa suka sanya ya"yansu atsakiya,Saleem ne yace"Duk ku tsaya yanzu kowa ya Fadi inda yake son Zuwa Hutu. "Da hanzari Ummita tace"Daddy ni da Sadiq Wajen Goggo Saleema zamu Hutu wannan karon mun barma su Ya aryan gidan Abbi.."Dariya yayi kafin ya kalli Khalipa yana Fadin"Babban yaya kai ina zaka..? Mirmishi yayi yana Fadin"Daddy gidan Daddi na zani nidai kasan bana chanji gidan Hutu.."Kansa ya Shafa yana Fadin"God boy,dama Ai Shima takwaran naka sonkai yake Nunawa,yafi son Zuwanka Fiye dana kowa.."Malika ne tace"Hajajju ke ina zaki Hutu ko zaki zauna damu.."Saurin girgiza kai tayi tana Fadin"No Momy gidan Goggo Saleema zani.."Da Sauri Ummita ta zaburo zatayi mgana Saleem ya dakatar da ita ta hanyar Rike ta yana Fadin"Ke wlh kin gado mai Sunanki sam baki da Hakuri.."Yafada yana Dungure mata kai,Kwabe Fuska tayi ta koma tana Hararan Hajiya,Malika ne tace"Toh Duk ku tsaya naga duk kuna Neman guduwa ne bamai tsayawa Wajen Goggo balle Wajen Anty Marym.."Dukkansu suka cuno baki suna bazasu tsaya ba,goggo Hadiza na Dariya tace"Allah Raka taki gona nima wlh na gaji da ku ku kara gaba gida yamana Shuru.."Malika Ta murmusa tana Fadin"Kyelesu goggo ai ke dama Uwar Malika ce,kinga duk zumudin nan da Sukeyi gidan Ummi zasu ci burgi don Jiya da daddare duka Daga gidan Goggo Saleeman har Gidan Daddi Marwan din Sun sauka gidan Ummi.."Jin haka yasa suka saka ihun murna Suna Fadin"Da gaske Mommy.."aiko amsa bata basu ba Suka mike kowanne ya Dauki akwatinsa suka Bi hanyar Fita suna Fadin"Daddy,mommy goggo,Mun tafi gidan Ummi,Achan zamu yi Hutunmu sai kunzo.."Suka Fada Suna Ficewa Harda Hajiya wacce ta Tashi Daga Hannun Malika ta bisu da gudu,Iyayen nasu suka bisu da kallon Sha"awa da kauna,Waje sukayi Dole Direba ya kwashesu amota Zuwa Gidan Ummi don sun matsu suga yan"uwan nasu musamman ma Ya Ayda Wacce ke Nesa,gwamma Su Ya aryan suna ganinsu in sunje Gidan Ummi ko kuma In su sunzo gidansu Duk da ba kasafai suke Zuwa ba. Da mirmishi afuskar Saleem ya Waigo yana Kallon Goggo Hadiza yake Fadin"Goggo ki Shirya in mun karya zamu Wuce gidan Ummi.."Mikewa tayi tana Fadin"Tohm bari na Hanzarta ai yan Wutar ciki Sun tafi Su.."Tafada Tana Dariya. Sai da ta Fita Afalon kana Saleem ya Manno Malika da jikinsa yana Shinshinar Wuyanta lokaci daya yana Shafa maranta Zuwa Cikinta,Dariya tayi tana Danna kanta bisa kirjinsa cikin Wani yanayi tace"Mallam,meka ke Bukata ne.."Akunne yayi mata Rada.."Ciki nake so nayi miki.."Ido ta zaro ta dago tana kallonsa cikin Mamaki tace"Ciki wani iri..?Kumatunta ya Shafa yana Fadin"Cikin Haihuwa mana Amanata,Hutun ai ya isa haka yakamata ama Hajiya kani ko kanwa.."Yamutsa fuska Malika tayi tana Fadin"Haba Daddy wani irin ciki kuma Ai ni gama kuma.."Wani kallo yayi mata kafin yace"Ko..? Saboda kinga na daga miki kafa kwana biyu ko..? Bari na Nuna miki har yau ina nan da karfina Insha Allahu kafin mu Tafi gidan Ummi yau sai nayi ajiya acikinki.."Yafada yana Kallonta ido cikin ido,Kwabe Fuska tayi zatayi kuka kawai taji bakinsa cikin nata,yana kissing dinta cike da kwarewa,itama Tallabeshi tayi Tana bashi Hadin kai,sai da yagaji don kanshi ya saketa yana Ajiyar Zuciya Kura ma juna ido Sukayi kafin Malika tayi Lum da ido ta koma Bisa kirjinsa tana Fadin" _Ina alfahari dakai Mijina...A komai na Malika malika kaci gaba da Ramuwa Har Abada.._… Dariya ya saki yana Sumbatar Saman kanta Kafin ya Mike ya Dauketa Cak ya Fara Tafiya da ita Zuwa sama inda Master Bedroom dinsu yake,Kallon Cikinta idonta yake yana Fadin" _*MALIKA MALIK SAI NA RAMA...Ammh bana Ramuwar da yawa Saboda Wani lokacin in Na rama ni nake Ramewa..*_ Dariya ta kyalkyalece mai dashi shima yana Tayata ahaka suka isa cikin makeken dakinsu da kafa ya Bude kofar suka ci burgi bisa Makeken gadonsu Cike da Kauna da Muradi mai girma Suke Gudanar da komai har abada bazasu gaji da juna ba,Kowani lokaci suka kebe kowannensu yana kokarin Farantama Dan"uwansa ne,wannan itace Kauna ta Gaskiya wacce ko man Tsufa bata yankewa har Gaban Abada. *TAMMAT BIHAMDULLAH* *GODIYA TA TABBATA GA ALLAH (SWA) WANDA DA IKONSHI NE KOMAI KE FARUWA,KAMAR JIYA NE MUKA FARA MALIKA MALIK,GASHI YAU 05/03/2020 NA RANAR THURSDAY,MUKA KAWO KARSHENSA HAKIKA DUKKAN GODIYA TANA WAJEN ALLAH DA MANZONSA SALALLAHU ALAIHI WASALLAM,TARE DA IYALANSA DA KUMA SAHABBANSA* _*Godiya ta musamman gareku *MALIKA MALIK PAID GROUP* da kuma *HAFNAN AND JANAF PAID GROUP* Bisa kaunar da kuka Nuna min wajen Siyan Littafina kuma ku ke Bina da Sharhi,Nagani kuma na yaba ina muku godiya tare Da Fatan Samun Cigaba arayuwarku ta Duniya gabadaya ina Rokon Allah ya Rabamana Ladan da mukayi dani daku wajen Rubuta Daidai acikin wannan Lbrin ya kuma yafemana Kura kuran da muka aikata Acikin wannan Rubutun,Allah ya saka muku da gidan Aljannah Firdausi Hakika Kalaman bakina yayi Kadan Wajen Mika muku Godiyata sai da Na bar Allah Shi zai biya muku Abunda kuka Man..Allah ya jikan magabata ya kuma Barmana Zumuncinmu Har Gaban Abada Ni Janafty Uwar Ladingo ina muku So Filla babu algus..*_ _Assalamu Alaikum Janafty Freeking Fans ga wani Albishir danake Tafe muku Dashi na Wani Sabon Lbrina mai Tafe da Sabon Salo wanda Zai Taba zukata wannan karon salon ba irin na bayane,Banta ba Dora alkalamina da irin wannan Salon ba,Na tabbata lbrin *ZAMAN GIDANMU..!* Mai cike da kunci Zai Taba Zukata dadama,Ma'u Yarinyace kin kowa kin wanda ya rasa wacce tatasO Acikin gidansu mai Tarin ya"ya ammh sai aka wayi gari Kannenta da Suke Kasa da ita Sunyi Aure Sun barta bawai don Bata da kyau ko tana da Wani Nakasu ba,sai don Ita nata Jarabawan Rayuwar kenan,Ta Fuskanci Tsangwama da Tsana,Kafin Allah ya Bata miji na Nunawa Jarida Burin kowacce mace,Ammh sai dai kash Nan din ma bata yi Dace da samun Jin Dadin da kowa yake Mata Fata ba,domin Abdallah Bashi da Ra"ayin kansa sai Abunda matarshi wacce ta mallakeshi dashi da Dukiyarsa gabadaya tace,ta Rabashi da kowa nashi Hatta da Uwar data Duka ta Haifeshi ta rabashi da Uban daya zama Ginshikin kawoshi Duniya ta rabashi da duk wasu abokananshi na Gari da yan'uwanshi ya kasance yana Rayuwa Wajen Bautama matarsa da yan"uwanta Saboda sakacinsa da kuma lalaci wajen addu"a,Kwatsam Rana Tsaka Ma"u ta yanki Tikitin Shigowa Rayuwarsa batare daya sani balle sanin ita matar tashi,Ma"u zatayi gwagwarmaya Sosai Zata Sha Wuyar RayuWa Sosai,Zata Samu Nasaran kwato Abdallah daga Hannun Muguwar matarshi..? Ko kuwa zata Samu Nasaran Rabashi da Wata karuwa wacce tayi Nasaran Shiga Rayuwarshi Saboda Sakacin Matarshi...? Duka Wadanan Amsoshin zaku Samesu ne ta Hanyar Biyan Naira 300 kachal ta wannan Account Nombar kamar Haka 0552179550 JAMILA UMAR GTB bayan kin Dauki Hoton Trancsation din kin Turo kai Tsaye ta wannan Nombar, 09069067488 ko kuma katin Waya na Mtna ta Wannan Layin 09069067488 Bayan kin Dauki hoton katin Kin Turo kai Tsaye,Ina Maraba daku Masoyana masu Son Cigabana kada ku Manta akwai Free Buk dina zai Fita Bayan Sallah insha Allah..._ *Gaisuwar ban Girma gareku*👇 _Sahiba Hafnan_ _Sisinah Aisha Alto_ _Momyna Anty Hauwa_ _Dota ta Ladingota.._ *ALLAH YAYIWA RAYUWARKU ALBARKA YA KUMA DAFA MUKU FIYE DA YADDA KUKE DAFAMUN..Ameen* _Janafty Aka Shakira ke Cewa BISSALAM_👏🙌 *_SHAKIRA_* *_JANAFTY*_ _*MOMYN LADINGO*_ _*ANITHA*_ _*SUNIATIN*_ 🔥🔥🔥🔥 E-book Creater by Sardaunah 08066046091