Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    “Alhaji…”

    “Zan saɓa maka.”

    Ba yadda ya iya. Cikin minti shabiyar ya sama musu tasi su huɗu suka kama hanya. Mama da Inna ba su san me ake ciki ba. Shi kuwa Alhaji tunda yaga sunan makarantar a bakin gate jikinsa ya soma tsuma. Ahmad dai jikinsa duk ya mutu. Ya yi kiran Taj ɗin da su ka shiga bai ɗauka ba. Da tambaya su ka ƙarasa wurin da ake gasar inda mutane su ka yi dafifi kamar ƙudaje. Basu wani sha wahala ba su ka hango tebura huɗu na ƙasashen da su ka rage a gasar. A yau za a fitar da wani team ɗin sai ya rage uku. Washegari idan an yi na ƙarshe a fitar da na ɗaya, na biyu da na uku.

    Cikin wata irin nutsuwa da tsantsar ƙwarewa Taj yake aiki. Shi da Wakili girkinsu cikin tsari yake kamar sun manta da lokacinsu na tafiya. Wannan nutsuwar ita tafi burge alƙalan gasar. Masu sauri saurin cimma lokaci kuwa daga kwano ya faɗi ya fashe sai ka ji su na washhh, mai ko ruwa mai zafi ya fallatso mu su saboda garaje.

    Tunda Alhaji ya yi tozali da ɗan nasa wani abu mai masifar ɗaci ya sami wurin zama a maƙogaronsa. Taj yake gani sanyi da dogon wando baƙi da riga yellow mai tambarin makarantar sai apron fari tas ɗaure a ƙugunsa. APRON!?

    Inna kuwa tamkar wadda aka watsawa ruwan zafi. Tunda ta nunawa Mama shi bata sake iya cewa komai ba. Maman ce ma ta iya yin magana da ƙyar.

    “Ahmad me idona yake gani?”

    “Gasar girki ce” ya bata amsa a sanyaye.

    “Ku zo mu koma.” Alhaji ya ce da matansa “Kai kuma ka jira ya gama ka taho min da shi.”

    Ahmad ya so raka su amma ya nuna masa yawo a ƙasar da ba tasu ba, ba baƙon abu bane gare shi. Haka su ka tafi babu mai cewa komai. Da isarsu Alhaji ya ɗauko magungunansa na hawan jini ya watsa sannan ya ce kada wanda ya tashe shi sai Taj ya iso. Dama ɗaki uku ya kama musu. Sai su ka koma ɗayan.

    Ido cike da ƙwalla Inna ta ce “Yaron nan so yake ya jaza mana tashin hankali ko me?”

    Kallonta Mama tayi ta girgiza kai.

    “Matsi da takura yaro bai fiye haifar da ɗa mai ido ba. Taj ya yi masa biyayya an sami abin da ake so. Mene ne aibu don ya ɗan waiwayi burinsa? Don fa mun haife su ba yana nufin dole su rayu kwatankwacin tamu rayuwar ko ra’ayi ba.”

    “Kayya dai Mama. Rayuwar yara sai da nuna hanya daga iyaye.”

    “Nima ban musa ba. Amma babu inda addini ya bawa iyaye damar tauye ƴaƴansu akan abin da bai saɓawa addinin ba. Baki ji malamai suna faɗin ko sakin aure indai ba bisa adalci ba, iyaye basu da hurumin tilasta shi ba? Girkin nan kuma maza nawa ke yi? Mene ne aibu a ciki tunda ba daudu yake ba?”

    Inna dai duk a tsorace take ta ce “tunda mahaifinsa ba ya so sai ya haƙura ko don neman albarka.”

    Mama gani tayi cigaba da nunawa Inna illar takura tayi yawa ga ɗa mai biyayya bata da amfani ba sai taga Innar ta kasa fahimta. Idan ta matsa kada abin ya yi kama da tana son sanya shi yin bore. Zaman jiran tsammani su ka yi har bayan Isha.

    *
    Sakamakon gasa yau dai da su Taj ya tashi. Cikin nasara da taimakon Allah su ne su ka yi na ɗaya. Yawan makinsu idan an haɗa da na kwanakin baya ya basu damar iya yin na ɗaya gobe in sun dage. Banda ihun murnar ƴan Nigeria da su ke makarantar ba ka jin komai. Yanzu ya rage teams uku. Gobe za a fitar da na ɗaya, biyu da uku. Da su ka fito za su tafi Wakili ya tare shi da godiya.

    “Ban san a ina ka koyi girki wanda yasa talent ɗinka ya zarce na kowa a nan ba. Your are truly amazing.”

    Taj ya yi murmushi “ai ban kai ka ba.”

    “Magana ta gaskiya ake yi. Idan muka yi nasara na san albarkacinka na ci. Saboda haka ina roƙonka don Allah gobe ka dage fiye da kullum. Samun karatun ya fiye min akan kuɗin da za a bawa na biyu ko na uku.”

    Murmushi Taj ya sake yi da alƙawarin in sha Allahu gobe zai yi bakin ƙoƙarinsa.

    Da tallafin gwamnati Wakili ya sami tahowa karatu. Ya gama degree kamar Taj amma yana tsoron komawa gida yanzu. A ƙauye su ke. Gashi samun aiki yanzu ya koma wa ka sani, wa ya san ka. Tunda yana aiki a wani gidan abinci a nan yana samun abin turawa mamansa da ƙanne ba zai so ƙarewar visa yasa shi komawa gida a sake naɗe hannuwa ba.

    *

    Murnarsa ta koma ciki da Ahmad ya faɗa masa tare da su Alhaji su ka zo akan hanyarsu ta zuwa hotel ɗin.

    “Yaya don Allah kada ka sanar dashi zancen competition ɗin nan.”

    Cije leɓe Ahmad ya yi wanda yasa Taj tambayarsa ko ya faɗa hankali a tashe.

    “Tare mu ka shiga inda ku ke girkin. Ya riga ya gan ka.”

    Bayan karanto duk wata addu’a da ya sani ta neman sauƙi, bai sake cewa komai ba har su ka isa hotel ɗin. Kai tsaye ɗakin Alhaji su ka je su ka tarar da Inna da Mama a zaune jigum. Jikin Alhaji har ya soma tsananta saboda damuwar da ya sanya a ransa.

    Wuri ya samu kusa da Mama ya zauna jikinsa a matuƙar sanyaye. Shiru yana jira a fara yi masa faɗa amma babu wanda ya yi magana. Cike da fargaba ya rarrafa gaban Alhaji kai a ƙasa.

    “Don Allah…”

    Tassss. Alhaji ya tsinke shi da marin da ya gigita shi. Inna tsam ta miƙe ta fice daga ɗakin don ba za ta juri gani ba. Ko da ta koma ɗaya ɗakin fashewa tayi da kukan da bata san na mene ne ba. Tana tausayin ɗanta. Tana kuma son ya sami damar cikar buri sannan kuma tana so ya yiwa mahaifinsa biyayya.

    Sake ɗaga hannu Alhaji ya yi zai kuma marinsa cikin zafin nama Mama ta riƙe hannun da sauri.

    “Ka dubi Girman Allah kayi haƙuri.”

    “Ki sakar min hannu” ya miƙe tsaye da fushin da yafi na farko yana mai fincike hannunsa.

    “Haba Alhaji. Mene ne aibun girki a wurin namiji da har za ka kasa bawa yaron nan damar cikar burinsa.”

    “Buri? Buri fa ki ka ce A’i?” Ya nuna ƙirjinsa “ɗan cikina ki ke so na bari ya yi daudu?”

    A hasale ta bashi amsa saboda har ga Allah tana ganin da gangan kawai yaƙi fahimta balle ya sassautawa ɗan.

    “Mece ce alaƙar girki da daudanci? Maza nawa ka gani da wannan sana’ar kuma ba su lalace ba? Ka kyautata masa zato mana ka bi shi da addu’a.”

    “Ni ki ke ɗagawa murya?”

    Ko ɗar bata ji ba ta ce “Gorin haihuwar namijin za ka sake yi min?”

    Ahmad ya fice kiran Inna. Taj kuma jin yadda rigima take son tasowa tuni ya dawo daga duniyar raɗaɗin marin da aka yi masa.

    “Mama bashi haƙuri mu fita.” Ya durƙusa a ƙasa “in sha Allahu nima ba zan sake tada maganar nan ba.”

    Hannun Mama ya ja su ka haɗu da Inna tana dawowa ɗakin da jan ido. Ganin sun fito ita ma ta bi bayansu ita da Ahmad.

    Kamar wancan lokacin yanzu ma nasiha game da mahimmancin yiwa iyaye biyayya su ka yi masa. Ya kuma karɓa hannu bibbiyu da zuciya ɗaya.

    Ƙarfe goma da rabi na dare saƙon Wakili ya shigo wayarsa. Tuni akan fitowa da wuri ya soma yi masa. A ƙarshe kuma ya yi rubutu kamar haka.

    “…My mum said we should keep reciting this Du’a tonight being friday night and tomorrow when the competition begins. RABBI INNI LIMA ANZALTA ILAYYA MIN KHAIRIN FAQIR. I will continue to thank Allah for bringing you my way no matter the outcome. Working with a pro like you is truly an honour. Thank you Happy Taj.”

    Duk iya sata ta bacci daidai da sakan guda Taj bai runtsa ba. Shaf ya manta ba shi kaɗai bane a gasar har ya yiwa su Inna alƙawarin haƙura. Gashi daga cikin dokokin gasar duk wanda abokin girkinsa bai zo ba har aka fara da minti goma sha biyar sun zama disqualified. Anya zai iya samun kwanciyar hankali idan ya zama sanadiyar rugujewar rayuwar wani?

    Kafin asuba babu irin tunanin mafitar da bai yi ba. Yana idar da sallah ya fice daga hostel zuwa hotel ɗin su Alhaji. Bai tsaya neman abin hawa ba saboda ƙarancinsu a wannan lokacin. Sannan babu wata tazarar azo a gani ma. Da gudu gudu ya isa yana faman haki. Kai tsaye ɗakin Ahmad ya fara zuwa. Da ba a buɗe ba ya durƙusa a bakin ƙofar yana mayar da numfashi.

    Zaman kimanin minti shabiyar ya yi sannan Ahmad ya dawo.

    “Lafiya me ya fito da kai da asussuba haka?”

    “Alhaji yana ɗakinsa? Ya tashi?” Taj ya tashi ya ma manta da gajiyar jikinsa.

    Yanayinsa na rashin nutsuwa Ahmad ya fara dubawa kafin ya shige masa gaba zuwa ɗakin Alhajin. Shi kaɗai ne a ɗakin don matan nasa sun yi yaji saboda abin da ya faru jiya. Sanye yake da farar jallabiya yana fitar da daddaɗan ƙamshin turaren larabawa. Gemunsa mai sirkin fari-fari da baƙi ya ƙarawa fuskarsa kwarjini. Kamanninsa da samarin ƴaƴan nasa ta sake bayyana.

    Gaishe shi Taj ya yi ya faɗi buƙatarsa kai tsaye. Ahmad na ji ya fita da sauri ya kira su Inna don su dakatar dashi kafin maganar ta lalace. Sun shigo daidai lokacin da Taj yake cewa,

    “Ba don kaina nake son zuwa ba. Nayi maka alƙawarin ko na nawa mu ka yi ba zan karɓi komai daga gare su ba. Izini kawai nake nema kada rashin zuwana ya zama silar rushewar ….”

    “Tajuddin!”

    Durƙusawa ya yi duk da kiran sunan nasa ya kiɗima shi cikin ƙanƙan da kai ya shiga magiya kafin ma ya ji me Alhajin zai ce. Wannan ya ƙara tunzura mahaifin nasa sosai.

    “Indai ni zan yi maka izini to ka sani har abada ba zan taɓa yarje maka ka sake tsayuwa gaban murhu ba. Allah Ya yi min rufin asirin da ko mata cikin tsatsona ba za su nemi kuɗi da girkawa wasu abinci ba balle kuma namiji.”

    Ƙwalla mai zafi ta shiga saukowa Taj a yayinda yake jin kamar da gayya mahaifin nasa yake tauye shi. To amma ko zai hana saboda baya son a haɗa ɗan cikinsa da sana’ar girki me yasa ba zai duba cewa rashin zuwansa zai salwantar da mafarkin cigaban ɗan marayan da bashi da gata ba.

    “Alhaji ka yiwa Allah…”

    “Na gama magana” Ya furta da izza sannan ya fuskanci Ahmad “ka canja mana booking idan akwai jirgi mu tafi yau da ƙanin naka. Takardunsa kuma ka tsaya ka karɓar masa.”

    Hankalin Taj tashi ya yi ya miƙe da sauri “Alhaji na rantse maka ba don ni zani ba. Idan ban je ba za ayi disqualifying ɗinsa.”

    “Wannan nauyin sai ya zame maka darasin rayuwa a gaba ta yadda ba za ka sake marmarin saɓawa umarni na ba.”

    Inna da Mama har ma da Ahmad saka baki su ka yi wajen lallashin Alhaji akan ya amince amma ya yi biris da su. Taj kuwa kuka yake tamkar yaron goye. A wannan yanayin wayar Wakili ta shigo masa. Alhaji da kansa ya ce ya ɗauka kuma ya faɗa masa ba zai je ba.

    “Happy Taj yi haƙuri na kira ka da sassafe.” Ya yi magana da ɗan jin nauyi.

    “Kada ka damu na riga na tashi.”

    Wakili ya yi ƴar dariya “jiya wanda mu ka gaisa ka ce yayanka ne ko?”

    “Eh.” Ya amsa da sanyin murya.

    “Breakfast na haɗa masa nake neman address ɗin ka. Na rasa da me zan karramaka. Ko a wannan matsayin mu ka tsaya kai ne sila. Zan so yin aiki tare da kai nan gaba.” Ya sake dariya “kana burgeni ne. Ina son koyon girki kamar kai.”

    Kasa cewa komai Taj ya yi sai ruwan hawayensa da ya ƙaru. Daurewa ya yi ya ce da Wakili zai tura masa address ɗin yanzu. Bayan ya ajiye wayar ya dubi Alhaji da ya gama jin komai.

    “Ka gani ko Alhaji? Yana da kirki kuma maraya ne. Cutar shi zan yi idan ban je ba.”

    Gajiya Alhaji ya yi da magiyar dukkaninsu ya ɗaga murya ya ce ce “Ku fitar min daga ɗaki gabaɗayanku.”

    Iko da izzarsa ba tun yau su ke damun Mama ba. Amma wannan ya fi ɓata mata rai. Wace irin zuciya ce da shi da za a dinga roƙonsa akan tallafawa rayuwar wani ya turje a kai. Sannan da girmansu ya haɗa su da ƴaƴan cikinsu ya yi musu kora irin wannan ta ƙasƙanci. Ta dubi hawayen Inna wanda ko ba a faɗa ba ta san na son share damuwar ɗanta ne. Bata cewa kowa uffan ba ta fita ta koma ɗaki inda ta baro wayarta. Kimanin minti goma ta ɗauka wurin yiwa mijin yayarta wanda ya kasance babban wa ga Alhaji ta fayyace masa komai.

    “Zan kira shi yanzu. Kashe wayar.” Kawai ya ce bayan ya gama jin bayaninta.

    Da ta koma ɗakin yadda ta fita ta barshi haka ta same shi. Saboda halin da Alhaji ya sanya jama’ar ciki hatta iskar ɗakin bata daɗi. Shigarta ke da wuya Alh. Jafaru ya kira shi kamar yadda ya yi mata alƙawari.

    “Hayatu.”

    “Na’am” ya amsa da ladabi domin ya yarda da aka ce babban wa uba, musamman wanda ya riƙe matsayin da gaskiya da amana irin yayansu.

    “Ni Jafaru na bawa Tajuddin izinin fita yaje ya ƙarasa abin da ya fara. Sannan ina mai umartarka da ka zauna har a sallame su daga makaranta ku taho tare.”

    “Yaya Babba?”

    “Idan ban isa ba kana iya take umarnina ka ɗora naka.”

    Bai bashi damar sake cewa komai ba ya kashe wayarsa. Alhaji ya kalli Mama da wani irin ɓacin rai mara misali. Sanin bata da gaskiya sai ta sadda kanta ƙasa kawai.

    “Tashi kaje wurin gasar.”

    Iya abin da ya ce kenan ya fice daga ɗakin ya barsu. Taj bai ma gane dashi ake ba sai da Mama tayi masa magana. Ya kalli agogo yaga takwas saura mintuna ƙalilan. Gashi da ƴar tafiya zuwa makarantar. Tunanin wanka ko kusa bai zo masa ba ya fita da gudu-gudu ya sauka neman abin hawa. Ya isa tara saura minti bakwai. Har an gama shirya komai sauran teams biyun sun tsaya suna jiran lokaci. Wakili kuwa shi kaɗai ne a can gefe yana ta baza idanu cikin tashin hankali.

    Taj na shiga wurin aka kaure da ihu da tafi. Ashe ba Wakili kaɗai ke jiransa ba. Masu mara musu baya da dama sun shiga fargabar makomarsu da aka ga bai zo ba. Tara daidai aka buga wata ƙatuwar ganga wadda ta bawa participants ɗin damar farawa.
    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!