Rayuwa Da Gibi – Chapter Eleven
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
Numfashi ta sake saukewa a hankali bayan ta karɓi loudspeaker ɗin sannan ta rufe ido ta buɗe da sunan Allah. Da ido ta lalubo Taj wanda har ga Allah tayi matuƙar mamaki da ta iya gano shi a cikin mutane. Bata sani ba ko hakan yana da alaƙa da sahun gaba da ya dawo ya tsaya a jikin ƙarfen canopy bayan kusan kowa a zaune yake. Ya yi mata murmushi gami da gyaɗa kai kamar mai bata damar yin magana.
Mantawa tayi da kowa da komai ta yi taƙaitaccen speech ɗinta mai ma’ana wanda kalmominsa su ka dinga zuwa kamar daga sama. Wuri kuwa ya kaure da tafi. Ɗalibai ƴan ajinsu su ka dinga kiran sunanta da ƙarfi suna tafi. Haka kawai tauraruwarta ta ƙara haske a idanunsu tun bayan da ta kare martabar iyayenta.
Idanunta lokaci lokaci su na kan Taj har ta gama. Tana addu’ar gamawa taga Taj ya kalli wayarsa sai ya kara a kunne ya bar wajen. Za ta sauka aka dakatar da ita. Mai Girma hakimin Gabasawa da kansa ne zai bata kyaututukan da aka tanada dominta. Wani ƙayataccen kwando ne aka saka komai aka lulluɓe da ledar ado aka ɗaure. Ya miƙa mata aka yi musu hoto tare sannan ya ce tasa kyautar ita ce kujerar Makka a Hajjin shekara mai zuwa in sha Allah.
“Allahu Akbar” Malamin da yake MC ya faɗi, sai ɗalibai da iyayen yara su ma su ka amsa.
Murna a wajen Hamdi kuwa ba a cewa komai. Ta sauko daga stage ɗin idanunta cike da ƙwallar zallan farinciki. Wurin da su Sajida su ke zaune ta nufa da sauri. Banda Sajida da Zee harda ƴaƴan ƴan uwan Abbansu mata tsararrakinsu. Halifa ma ya baro ɓangaren maza aka yi murnar tare da shi.
“Hamdi ina kayanki? Yaya ta ce kada mu yarda mu wuce ƙarfe biyu nan.”
Halifa ya ƙara da cewa “ana can ana haɗa miki …”
Kafin ya gama magana Zee ta dage ta doke masa ƙeya.
“To fesal uban zance.”
Hannu Hamdi tasa ta saƙalo kafaɗarsa tana dariya “rabu da ita Halifa. Idan ka faɗa min me ake yi zan bar maka duk ragowar provision ɗina.”
Da sauri Zee ta riga shi faɗa.
“Walimar ƴan gida za ayi miki”
“Kin dai ji kunya wallahi. Da kayan ƙwalama za a sayeki cikin sauƙi” cewar Sajida tana taɓe baki.
Kayan nata ta nuna musu su ka haɗu da cousins ɗin nasu aka kwaso cikin ƙanƙanin lokaci. Ta koma cikin ƴan uwanta ɗalibai aka yi hotuna harda malamai da musayar lambobin waya. Wasu harda kuka sosai. Ita dai bata yi ba don sabon da tayi da abokan karatun nata na iya lokacin jarabawa ne. Kewar rayuwar makaranta tafi damunta.
Duk abin da take yi hankalinta yana komawa ga tunanin ina mutumin nan na ɗazu. Ta gaji da juyawa ko za ta gan shi Allah bai yi ba. Ga Sajida ta damu su tafi don ita za a yiwa faɗa idan su ka ɓata lokaci. Haka ta tafi zuciyarta tana begen sake ganin sa.
*
Wayar Amma ce ta sake shigowa, ita ce dalilin da yasa ya bar wajen. Kuka take yi wanda ya matuƙar tayar masa da hankali. Ta sanar dashi surukarta Hajjo ta ce lallai ta zaɓi tsakanin aure da aiki amma ba za ta haɗa biyu ba. Mijinta shekarsa huɗu da ritaya ya koma gida gabađaya.
“Wai zaman me nake yi a nan. Taji an ce kai ma ka dawo.”
“Ba ki faɗa mata ba daɗewa zan yi ba?”
“Nayi mata bayani duk taƙi ji. Yanzu don Allah 7 months to my retirement sai nayi resigning? An yi min adalci kenan?”
Ta maza ya yi bai nuna mata damuwarsa ba ya dinga rarrashinta. Da ƙyar ta haƙura bayan ya yi mata alƙawarin zuwa Abuja ya sami Hajjo a gidan mijin Amma ɗin inda take zama da amaryarsa da yaransa.
Yana dawowa cikin ƴan uwansa Firdaus ta janye shi tana ta nunawa ƙawayenta Uncle Taj. Daga hoto ɗaya sai da aka yi yafi goma. Masu ƙyasawa da yawa su ka kasa ɓoyewa. Shi dai ya biye mata ne kawai saboda ko a cikin jikokin gidan ita ce ƴar gaban goshinsa. Indai ana hutu tana yawan kiransa. Ana hoton da hayaniyar amma idanunsa yarinyar nan Hamdiyya Habib su ke nema. Da bai ganta zuciyarsa bata kawo komai ba tunda yana da yaƙinin Firdaus ba za ta kasa saninta ba. Bai san Hamdi bata da ƙawa ba. In ka cire sunanta ko sunan unguwarsu babu wadda ta sani.
***
Washegari jirgin ƙarfe bakwai ya bi zuwa Abuja. Idan buƙata ta biya so yake ya dawo a ranar don yanzu ya matsu ya koma wurin Amma. Da yake tun dare ya sanar da Daddy mijin nata cewa yana tafe, yana isa direba ya zo ya ɗauke shi.
Iyalan gidan ba baƙinsa bane tunda su na yawan kai ziyara America har Hajjo. Ƴan mata uku ne ƴaƴan kishiyar Amma da ake kira Anti. Su ma duka sun saba da shi. Dama tun zuwansa yana son tahowa Abujan su gaisa amma aiki ya hana. Tarba mai kyau ya samu daga Antin da ƴaƴanta. Sai da ya ci abinci ya ƙoshi sannan aka yi masa ido ɗakin Hajjo.
A hakimce kan kujera ya sameta ta kashingiɗa tana danna remote.
“Wannan zuwan na san na Jamila ne ba don neman albarkar tsofaffi ba.”
Taj ta sosa ƙeya “tuba nake Hajjo tawa ni kaɗai.”
Ƴar tsohuwar ta yatsina fuska “bana son daɗin baki. Ai da uwarka Jamila ce a gidan nan ba za ka saka aiki a gaba ka kasa zuwa ba.”
Anisa babbar ƴar Anti ta nuna rashin jindaɗin wannan furuci “abin kuma harda zagi Hajjo?”
“Fita ko ban guri ai ba kiranki nayi ba.”
“Ya Taj na biyo.”
Hajjo ta haɗe fuska tana neman abin duka “Duk gidan nan babu wanda ya isa ya yi min iko da ɗaki saboda haka get out.”
Taj da Anisa su ka saka dariya. Ita tana cewa “yeeyyyy, Hajjo ta tuno zama cikin turawa.”
“Zan zagi babanki wallahi. Zo ki fice.”
Kafaɗa Anisa ta noƙe ai kuwa Hajjo ta bita da daƙuwa hannu bibbiyu.
“Na iyayenki su uku.”
Alamun rashin jindaɗi Anisa ta nuna wanda Taj ya lura. Da ka ya yi mata ishara ta fita daga ɗakin.
“Hajjo sai ki yi ta zagar mana iyaye saboda Allah? Kinga bata jidaɗi ba daga ɗan yin wasa da kakarta.”
Lura tayi shima kamar bai jidaɗin ba sai kuma ta saki fuska. Ita a dole Taj ne kaɗai jikanta namiji na wajen babban ɗanta. Tunda ya koma hannun Amma bata taɓa canja masa ba. Saboda tun asali dama kakarsa wadda ta haifi Alhaji da ita ƙawaye ne da su ka yi ƴan matanci tare.
Ita ta fara zayyano masa ƙorafinta akan zaman Amma ita kaɗai a gida ga mijinta a wata uwa duniyar.
“Saura bai fi sati uku ba na koma in sha Allahu. Kuma zan zauna har tayi ritayar. Ai na san zamana ne sharaɗin da yasa ki ka yarda ta cigaba da aikin.”
Hajjo ta ƙara sakin fuskarta saboda Taj akwai iya tsara zance.
“Ka san ita mace bata tsufa da buƙatar kulawa. Yau ko ƙwan fitila ne ya mutu wata idan babu namiji a gidan sai dai ta zauna a duhu.”
Haƙuri ya sake bata da yaga ya samo kanta kuma ya yi mata bayanin gininsa da ya yi nisa.
“Shi uban taurin kan har yanzu baku daidaita bane?”
Dariya Taj ya yi. Kamar ba ita ta nuna ta daina ƴan mintuna ƙadan baya ba.
“An dawo kansa kuma?”
Ko a jikinta ta ce “Ai Hayatun ne akwai wuyar sha’ani sai ka rantse ni na haife shi. Don ita babar tasu haka take ba cas ba as.”
“Ahhhh. Ni fa Hajjo zan tashi wallahi. Harda kakata kuma.”
Yadda ya ɓata fuska sai da tayi dariya. Daga nan aka kashe maganar dawowar Amma. Sai kuma ta sako zancen da yake cin ranta. Dama can ba dawowar Amman bace a gabanta. Tafi kowa sanin halinta tunda a gabansu ta tashi. Ita ce ma ta haɗa auren nata da ɗanta. Da gangan ta tayar mata da hankali yanzu kawai don Taj ɗin yazo. Don tayi imanin indai yaji ba zai ƙasa a gwiwa ba zai zo neman sulhu.
“Tajo.”
Babu yadda ya iya. Dole yake amsa sunan nan da baya son a faɗi indai daga bakinta ne.
“Nace wai me zai hana ka nemi ƙanwarka Anisa ku daidaita? Karatunta sai gudu yake har an shiga aji huɗu a jami’ar nan.”
Gabansa yaji ya faɗi. Duk kirkin Hajjo kowa ya san rigimammiya ce ta buga misali. Yanzun nan sai ta yiwa mutum dabaibayin da zai sarƙe wuyansa bai sani ba.
Ƙofa ya kalla tana gama maganar “Hajjo daina faɗa kada ta zata gaske ne ta soma jin haushina don na tabbatar ba za ta rasa masoyi ba.”
Shan kunu tayi harda yi masa daƙuwa.
“Ƙaniyarka Tajo.”
Ya sunkuyar da kai yana sauraron sababinta.
“Da akwai wanin ai ka san ni ba mai yiwa jikoki shisshigi bace. Sannan na tabbata da daga cikin Jamila ta fito ba ma za ka ce komai ba.”
Hankalinsa tashi ya yi ya miƙe tsaye yana ɗan tausar kafaɗarta.
“Allah Ya huci zuciyarki. Ba haka nake nufi ba.”
“Za ka yi mata maganar ko na kirata yanzu?”
Gani ya yi za ta rushe masa ginin da bai fara saka tubali ba akan yarinyar nan Hamdiyya. Shi yasa da saurinsa ya ce ta bari shi zai yi.
“Alƙawari fa za ka yi min.”
“In sha Allahu zan yi mata magana.”
Tana jin haka ta washe baki hankali kwance. A ranar da washegari da zai taho bata sake tada wata rigimar ba. Daddy kawai ta kira ta ce masa tayi mai wuyar. Ya fara shiri don ba za ta zuba ido ya bar ƴan mata a gabansa babu aure ba. Da yaji waye zaɓin da ta yiwa Anisa sai taga ya fita farinciki. Kuma da murnarsa ya kira Amma ya faɗa mata. Sai ta nuna masa ta fishi jindaɗi domin ita ba butulu bace. Duk wata gudunmawa da ta dace financially da morally ya bata wajen kulawa da cikar burin Taj.
***
Rayuwa ta fara tsanani ga iyalin Abba. Da yake mutum ne mai sakarwa iyali aji daɗi da abin da Allah Ya hore masa, yanzu da ajiyar ta soma ƙasa sai suke ƙuntata. Yawancin samunsa in ka cire buƙatun gida to anyi amfani dasu wajen tarin kayan ɗaki da yake yiwa ƴan matansa. Komai na mutum uku yake saya. Yaya bata san yiwa ƴaƴa komai ba ta wannan fannin don bata sana’ar komai. Tun da ƙuruciya babu irin nacin da bata yi ba amma sam yaƙi yarda tayi saboda a cewarsa ta gama aikinta da ta aure shi. Nan kuwa yana tausayin lafiyarta ne. A ganinsa rashin imani ne zai sa ya sanya rai da ta dinga neman kuɗi a yanayin da take ciki. Gashi dama bai tsira daga dariya da surutun mutane ba. Idan ya bari tana shiga jama’a da sunan sana’a babu mamaki a karyar mata zuciya da zancen lalurarta. Shi yasa ya yiwa tufkar hanci da wurwuri.
Sauƙinsu ɗaya yanzu a gidan shi ne kitson da Sajida take yi. Hamdi kuma satinta biyu da dawowa gida Anti Labiban Abuja da ta zo Kano ta roƙi alfarmar tafiya da ita idan za ta koma. Kowa ya san miskilancin Hamdi idan ta so. Suna ta zaton za ta ƙi. Sai gashi da kanta ta amince za ta bita. Weekend na zagayowa kuwa su ka tafi.
*
Abin haushi da takaici da Taj ya tambayi Firdaus game da yarinyar da ta kasance overall a makarantarsu wai bata san komai a kanta ba.
“Ba ƙawarki bace?”
“Hamdiyya ai bata da ƙawa ko ɗaya. Sai da case ɗin babanta ya tashi ne ma ta ɗan sake da mutane.”
Interest ya nuna na son jin me ya faru da baban nata. Firdaus kuwa ta zage ta kora masa jawabi tiryan tiryan. Har hukuncin da makaranta ta ɗauka akan ƙawayen Ummi tunda ita an cireta.
Tana gama jawabin ta tashi tayi gaba abinta. Ta bar shi da shiga ruɗani da mamaki. Ba kuma komai bane ya sanya haka illa tuna sunan mahaifin Hamdi da kuma sana’arsa da Firdaus ta faɗa.
Tunani barkatai ya shiga yi game da yadda aka haihu a ragaya. Indai shi ne Habibun da Alhaji yake ƙyamar ya yi koyi da halayyarsa to yaya aka yi ya yi aure? Me ya faru da rayuwarsa? Kuma wace irin rayuwa yake yi yanzu?
Tabbas zai so sani. Shi Tajuddin zai so ƙwarai ya shiga cikin rayuwarsa ba don ƴarsa kaɗai da ta tarwatsa masa zuciya ba. Wasu burika ne suka mamaye zuciyarsa wanda zai so ya cimma in har shi ne wanda Alhaji ya sani ɗin.
Kwana biyar kacal su ka ɗauka shi da Kamal wurin neman Habibu Simagade na Soron ɗinki. Sai gashi an kai su har ƙofar gidansa. Mutumin da ya rako su magidanci ne amma har su ka isa hirarsa akansa bata wuce alkhairinsa da kyakkyawar tarbiyar ahalinsa ba.
“Ai wato banda ance kowa da ƙaddararsa da in kaga wani aka ce maka zai sami sauyin rayuwa sai ka ƙaryata.”
“Me yasa ka ce haka?” Kamal da Taj bai ɓoyewa komai ba illa son Hamdi ya tambayi mutumin.
Shi kuwa ya daina tafiya tare da binsu da kallon rashin yarda. Sannan ya nuna Taj.
“Ka ce min kai sana’ar girki kake yi. Ɗan uwanka kuma kasuwanci.”
“Haka ne.”
Da faɗa-faɗa ya cigaba da magana “zamanin yanzu ai babu yarda a tsakanin mutane. Da naji aikin naka na zata taimakon Habibu ka zo yi. Shi yasa ma zan kai ku gidan.”
Taj ya yi murmushi “sana’ar girki yake kenan?”
“Watannin baya ba. Kafin ƴan hassada su sako shi a gaba su ka ƙwace wurin da yake haya. Banda haka ko garau garau Habibu ya dafa maka wallahi sai ka ji bambanci.”
Duk surutun mutumin nan bai ƙara yarda ya đara daga inda yake tsaye ba yana jiran su faɗa masa gaskiya ko su waye su sai ga Abba ya fito. Daga yanayin tafiyarsa da kamanni da ya gani da Hamdi Taj ya gane shi. Kafin ya iso wurin da su ke ya tsaya ya fi sau huɗu yana gaisawa da mutane. Wannan abu ya sake burge Taj sosai har bai san lokacin da haƙoransa su ka bayyana da farincikin da ya shiga ba.
MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
