Search
You have no alerts.
    The Den of Novels

    .Alhamdullahi mu dat na samun kulawa matuka
    daga bangaren ummi, duk abinda take so shi take mata
    ,sannan duk abinda ya dace mai ciki taci ko amfani dashi
    shi ummi take bata
    Sai da aka samu tsawon wata guda cur da rasuwar yaya
    akram ,sannan bunayya ya bayyanawa su dady labarin
    halin da Yaya akram ya tsinci kansa a dalilin rashin auren
    days so yi suka hana , har ma da labarin yaransa dake
    kasar Spain ,wannan dalilin ne yasa ya kamu da ciwon
    zuciya , bai tsaya iya nan da ba har sai daya labarta
    musu irin nadama da yayi da tuban da yayi kafin
    mutuwar ta riskeshi
    “dan haka shi ya yanke shawarar cikin satin zai Shiga
    kasar ,koda kuwa baza’a bashi yaran ba, amman at
    least dai yasan wani abu daya danganci akram ,mu
    musan inda ahlinsa suke
    Hankalin dady kusan yafi na kowa tashi a lokacin tunda
    bunayya ya soma mgn yake kallonsa tamkar hoto ,ya
    kasa kwakwarar motsi ,gabadaya so yake yaji
    zantuttukan bunayya sun zamo tamkar a mafarki ne
    suke Shiga cikin kunnuwansa, Amman yadda bunayya
    din ya Shiga fito da hotuna akram da yaransa da polina
    yana nuna musu ,daya daga cikin hotunan a bircth
    sukayi , wasu a wuraren shakatawa wasu a gida
    suna dry
    cikin farinciki ,varan masu tsananin kama dashi sosai,

    basu d’auko komai na polina ba sai Karin hasken fata.
    da kyar dady ya samu ya dinga furta kalmar “inna lillahi
    wa inna ilaihi rajiun yayinda tuni parlour’n ya kaure da
    kuka ,Kowa kuka yake mumy cikin kuka tace “duk son
    zuciyarka ne ya jawo haka….
    Kasa na rasa d’ana a dalilin banzar ra’ayinka ,yaro ya
    nuna maka aure yake so amman ka kekashe kasa kace
    Sam sai ya gama karatu , ai ga irinta nan kasa an haifa
    min jikoki ta hanyar zina .
    kuma a wata kasa wallahi
    Muhamud ka cutar dani ,ka cuceni cutar da har na mutu
    bazan manta ba
    ‘ummi ta Mike daga inda take ta isa inda mumy take
    zaune ta rungume akin kuka tace “kiyi hakuri aunty
    zuwaira , haka Allah ya kaddaro kowa da irin kaddara da
    Allah yake masa
    ,ki d’auka wannan jarabawarmu ce ,sai fatan Allah ya
    bamu ikon cinyeta ,kiyi hakuri gabadayanmu muyi
    kuskuren, “,dole nayi kuka mukarama ,saboda nima na
    biyewa son zuciyarsa ,na mance ni macece ,yanzu ina
    zan samu kmr akram?
    “yaushe zan haifi d’a kmr akram ?
    “a koda yaushe yana k’ok’arin kyautata min da yi min
    biyayya ,Allah dai ya gafarta masa yasa ya huta ,yasa
    karshen walahar kenan ,Allah ka hadasshi da malaikun
    rahma ,ya Allah kamar yadda kace aljanna yaya maza
    suna karkashin tafin kafafun iyayensu to ni Allah
    kagani na d’agawa akram tawa kafar , kasa aljannah ce
    makomarsa ta k’arasa fad’in hk tana wani irin kuka
    “a lokacin da maganganun mumy ke Shiga kunnuwan
    dady ,ba iya kunnensa kad’ai maganar ta tsaya ba, har
    zuciyarsa yake jin komai, kusan zaucewa yayi, ya dinga
    sambatu “shikenan ni na kashe d’ana da kaina, tun
    da’akayi mutuwar bai zubda hawaye ba ,sai na zuci
    ,Amman yanzu hawaye ne kwance a saman kuncinsa
    gabad’aya, ya dawo abun tausayi ,wuni ranar babu
    Wanda ya sakawa cikinsa komai kowa ka kalli fuskarsa
    (3
    ta kud’e saboda kuka
    Allah sarki mumy kwana tayi ranar da zazzafan zazzabi
    ajikinta ,Sam ta kasa runtsawa jin mutuwar akram take
    sabuwa agareta
    ,dana sani kuwa tayi shi sau babu adadi ,tayi nadamar
    biyewa son zuciyar mijinta ,shine duk ya janyo komai
    yayi tsanani a gareta, tabbas akram yaro ne mai ladabi
    da biyayya, ba zai ta’ba bijire umarninta bare na
    mahaifinsa ,”danasani na amince masa a lokacin dayazo
    da batun yana son yayi aure .
    da yanzu ya’yansa zasu zame min sanyi idaniya a gareni
    , kallonsu kad’ai zai rage min rad’adin rashinsa, bazan
    sakawa ranna soyayyar ya’yansa na wata uwa duniya ba

    ,domin kuwa da wuya uwarsu ta bari ta gansu shikenan
    bazataga jikokinta ba ?
    Tayiwa kanta tamvayar,
    wasu hawaye masu zafi suka zubo mata wannan
    zazzabi bai hanata tashi cikin dare tayi alwala ta Shiga
    sallah tana nemawa d’anta rahma gurin Allah
    Akwana daya dady yayi da wannan labari ,ya dawo abun
    tausayi ,Dan idan ka kalleshi sai ka tausaya masa ,Dan
    kuwa yayi kuka tamkar k’aramin yaro, har wata doguwar
    Rama yayi gabad’aya ya fita haiyacinsa , surutui ya koma
    yi ,kallo day’a zaka masa kasan baya cikin natsuwa da
    kwanciyar hankali, daman kuma dauriyar mutuwar kawai
    yake Amman a yanzu komai ya dawo masa sabo, har sai
    da mumy tazo tafi shi dauriya da tawakalli har ma daga
    karshe ta dawo bashi baki ,ummi ma tayi iya kokarinta
    dan gani ya samu natsuwa tare da bashi tabbacin za’a
    zo da yaran ,dady yayi wa kansa alkwarin ba zai sake
    takura ya’yansa akan karatun boko ba haka zalika
    yaransa mata duk aure zaYi musu ya hutawa
    rayuwarsa….
    Su ummi basu dawo Lagos ba sai bayan da akram yayi
    wata biyu ,lokacin cikin muwaddat ya Shiga wata na
    takwas ,tun da suka dawo muwaddat bata sanya
    bunayya a idanunta ba, yana can yana fama cikucukun
    Shiga kasar Spain , sai data samu tsayin wata daya
    sannan ya zo mata da labarin tafiyarsa ,zuwa kasar span
    , shi da yaya alameen acikin satin tabbas taji dadin
    kwarai da gaske ,sannan taji rashin jin dadin kartazo ta
    haihuwa baya nan, sai dai ta nuna bata damu ba sosai ,
    saboda gudun kar ya gane ya rusa tafiyar ,yace har sai
    byn ta haihu ,ita kuma abinda ba zata so kenan yaya
    ba,yaya akram ya wuce komai agurinta ,yafi komai a
    rayuwarta ,sanin inda yaransa har uku suke shine
    farincikinta
    Yau tsawon kwana Goma da tafiyar bunayya amman ko
    sau daya basuyi waya dashi ba ,tashiga damuwa sosai
    har damuwarta ta fito fili, kullun ummi na kwantar mata
    da hankali Wanda hakan ya rage mata tsananin tunanin
    rashinsa kusa daita ,hakan ba karamin dadi yakewa
    muwaddat ba gani yadda ummi ta sake maidaita yar
    gata ,bata aikin komai kayan data Cire sai dai a wanke
    Wanda zata sakawa jikinta ma sai dai ta gansu ,komai
    ummi ce ,shi yasa kullun take jin ummi ta zarce matsayin
    uwa gareta, ta zame mata komai na rayuwarta ,yanzu da
    ta gudu tabi uwa duniya a wannan ranar yaya rayuwar
    zatayi ?
    ‘Allah nagode maka da ka arzurta ni da samun uwa kmr
    ummi ,allah ka ja da ranta, ka kara Mata Nissan kwana
    ,samun irin su da wuya a wannan lokacin…
    Tana kwance a d’akin ummi saboda gyaran d’akin da
    zaayi ,karar wayar dake gefen gadon ummi ce ta tasheta
    daga baccin daya soma d’aukarta mai dadi ,cikin tsaki da
    yatsina fuska ta d’auki wayar ta manna a kunneta tare da
    fad’a “Assalamu alaikum “daga can bangaren aka amsa
    mata da waalaikas salam ,tana jin sautin sanyayyiyar
    muryar tasan sanyi idaniyanta, burin zuciyarta tsayayen
    namiji abun tikaho, nmjin dake shirin tafiyar da rayuwarta
    da komai nata, Muhammed Auwal kenan cikin sanyayyiyar
    muryarsa yace “na tasheki a bacci ko ?
    Bari na kashe kar NASA ki Haifa min yaro mai mannen
    ido tunda NASA shima baby bacci zai yi, ya fad’a cikin
    farinciki “Kamar kasani har ma da yankakken kunne tayi
    maganar cikin muryar shagwa’ba “sorry love banyi zaton
    kina bacci ba, ganin rana ce a fuwa zuciyata, ya baby nah
    ki fad’a baby kar yayi fushi yanzu ummansa zata koma
    bacci yayi hakuri inzo inganshi da kunnuwansa da
    idanuwansa ,suka sa dariya ,”kai bunayya bakagajiya da
    soyayya wallahi ,ya bakunta da fatar kunyi nasara?
    Baki ai sun kusan dawo wa ,to dai da dan nasara zance
    ,domin dai an sanar mata da komai tayi kukanta ta
    hakura, batun zuwa da yaran ne kam babu sauki, wannan
    sai dai zuwa wani lokaci idan sun girma kenan..
    Ni dai zanyi k’ok’arin ziyartasu akoda yaushe, saboda su
    sani su shaku dani, shine kawai hanya mafi sauki da
    zanyi domin sadasu da sauran yan’uwa dan bakiga
    macen ba muwaddat wallahi kmr kece kika haifeta ,sak
    kamarku day’a sauran mazan kuma yaya akram Allah dai
    ya jikansa “ameen tayi mgnr tana goge hawayenta “ba
    kuka zakiyi ba muwaddat mu godewa Allah ,dayasa ta
    fahimcemu, bata takaryata cewar ba yaransa bane da
    me zamuyi ?
    Muna nan dawowa cikin satin nan, nafi son ki Haifa min
    baby nah ina nan ,ina son ganin haihuwarki ,naji ihun
    first nit dinki zanso naji na haihuwa, shi Kuma kowa za’a
    Kira?
    Suka sa dariya gabad’aya “bunayya kenan har kasa na
    harareka a waya “kai kai to ina dawo kuwa sai na biya
    kudin harara da kudin da bazasu kirgu ba tasan irin
    kudin da yake nufi ,dan haka ta’ajiye wayar kawai
    Yau ta kama ranar dawowarsa tun asuba ummi tasoma
    shirya masa abinda zasu ci idan sun sauka ,ita kuwa
    muwa at tayi wan ata gyara ji inta ta awo turarru a
    tabi jikinta dashi domin shirin tarbo mijin abun har yaso
    yabawa ummi mamaki ashe datayi k’ok’arin aurar da
    muwaddat ga wani , tabbas da tayi kuskure ,maganar
    abi daya ce da zasu bi junansu ,yanxu ma da basu tare
    ba, suke bare bare, ina ga sun koma gidansu , kusan
    tafisu matsuwa tana gama shiryawa tashige cikin
    Bargon ummi tare da kashe fitila d’akin ta kwanta wani
    bacci mai dadi ne ya d’auketa
    Karfe takwas da rabi na safe taji tashin sautin muryarsa
    a daf da shigowa d’akin ummi tayi saurin juyawa kofar
    baya a dole bacci takeyi .
    Tana jin shigowarsa har da mayar da kofar ya rufe da key
    a zuciyarta tayi dariya shi kuwa har wani sanda yake wai
    kar motsinsa ya tadata ahankali ya haye gadon ya zauna
    daidai inda ta mayar da fuskarta .
    Take zuciyarta tashiga dokawa ta dinga kokuwa da
    numfashinsa, lokacin dataji ya sumbaci lips dinta ,ya
    gangaro zuwa cikinta shima yayi masa kiss tare da Dan
    shafawa alamun ko yana cikin koshin lfy ,sai lokacin ta
    bud’e idanunta Dan kar ya zarce daga hkn, dan tasan
    hali, ita dai kam sai dai tabawa wani labarinsa ,ahankali
    ta tashi zaune tana yatsina fuska ,ya matso kusa daita
    sosai ‘Sannu na tasheki ko ?
    Kafin tace wani abu ya rungumeta ajikinsa yana murnar
    ganinta da kyar ta samu tarabata da jikinsa ya kamo
    yatsun hannuta “,ya baby nah ?
    Ni na isa, ayi min afuwa ya kike kin tashi lfy?
    Lafiya lau ya kuka baro min yarana fatan duk suna cikin
    koshin lfy?
    “Alhamdullahi duk suna lafiya kmr mu barosu har
    airport suka rakomu su da mamansu abun tausayi .
    Yana maganar yana shafa fuskarta zuwa cikinta cikin
    minti ashirin tasoma jin bakon alamari na maganarsa da
    ta canza salo zuwa wasanin daita, ta soma
    Biye masa sukayi Amman acikin minti talatin taji
    bunayya na neman canja akalar wasa ,hakan yasa ta
    nuna masa alamar ba’a wasa biyu alokaci daya a kare
    lafiya ,amman take ya nuna mata shi mai iya wasa kala
    hudu ne a lokaci day’a, amman wannann wasan shima
    bazai iya ba adaidai wannan lokacin burinsa bai wuce ta
    haihu su tare a gidansu ba, ta tsura masa ido tana jin
    yadda soyayyarsa ta dawo mata sabuwa fil ta kai bakinta
    ta sumbaci fuskarsa,” ina sonka mijina, kmr ta tsira
    masa allura yayi wani firgigib ya cakumota ya kwantar
    ajikinsa ‘bunayya wai meye hk ?
    Sone aunty nah
    Bai barta haka ba sai daya auratayya daita ,iya murzuwa
    ta murzu a hannunsa .
    Wuraren misalin karfe tara na safe taji jikinta yana mata
    ciwo iri iri’ Amman hakan bai hanata hirarta da ummi ba’
    da binta mai aiki ba’ hkn kuma bata sanarwa da kowa ba
    har ta Mike tashige dakin ummi ta kwanta Cikin baccin
    Clwon mara a, al sa onu u a uguntaya ama ara
    da wani juyi ,baccin da bata koma ba kenan
    Cikin minti Goma sai gata a tsaye ciwo yayi tsanani
    wauta irintata, sai ta kwanta Amman ciwo ya gagara
    zama bare kwanciya
    cikin haka marata tayi wani irin Murd’awa ta saki wata
    razananniyar kara sai ga ummi tashigo a guje kmr zata
    fad’i tana ganinta tasan abun yazo.
    ta fita da sauri tsawon minti biyar suka shigo tare da
    bunayya, lokacin har faya ta fashe Sam ummi batasan ya
    biyota ba “,me haka bunayya ?
    Ko kulata baiyi ba ya ykarasa da sauri gurin da
    muwaddat take durkushe tana ciza lebe babu kunya
    bunayya ya kamota yana shafa gashin kanta zuwa
    bayanta ” sannu kuwa yayi mata yafi sau Goma sha
    gabadaya amatsayinsa na likita kasa aiwatar da komai
    yayi ,ummi tace tashi ka fita waje kabarta taji da Abu
    daya
    da kyar ya bar d’akin ya Shiga kai kawo atsakanin d’akin
    da parlour’n Amman har lokacin shiru babu labari aiko
    ya sake shigowa yayi zaman Durshan agabanta, ita kuwa
    tuni ta manta da sha’aninsa ,har ma da ummi sai kiran
    sunan Allah take ,da yan adduo,i ummi ta fita cikin sauri
    ta sake dawowa da sauri tana bashi umarni ya fita ,shi
    kuma sai magiya yake mata kada a barta ta mutu ,ummi
    ki taimaka mata mana , mata dayawa gurin haihuwa

    suke mutuwa .
    “dan Allah ki taimaka karta mutu kalle yadda take shan

    wahala muje hospital “ko hospital din mukaje iya abinda
    zan iya mata kennan, yanxu ta soma nakudar fa sai zuwa
    nan da awa biyu zata haihuwa “inna lillahi wa inna ilaihi
    rajiun ya furta awa biyu ummi ?
    ‘Ta Dan daga masa kai kawai ,ai awa biyu tazo ta wuce
    shiru da tafiya tayi tafiya ta Dan bud’e idanunta sai
    ganin bunayya tayi zaune a gefen gado yanata faman
    goge hawaye
    Muwaddat bata haihu ba ai data gama shan wahala,
    zuwa lokacin hatta ummi hankalinta ya tashi ,shinkuwa
    bunayya ma ya daina kuka ya zuba mata ido yana jiran
    yaji ance ta mutu domin ya sadaukar da mutuwa zatayi .
    Wuni zirrrr tayi durkushe tana abu daya Sai karfe Goman
    dare ta haifo yaronta nmj , acikin jinin da take tsugunne
    bunayya ya rarrafo ya rungumeta ajikinsa, yana mata
    sannu ,ya dinga furta sannu har sai da ummi ta rufe
    masa baki saboda yawon sannun dayake mata sannan
    ta d’auki yaron tayi bayi dashi.
    Da bunayya duk akayi aikin jini, sai da aka gama gyarata
    tsab ya ganta lafiya sannan yake tambayar ummi abinda
    aka Haifa ummi ta d’auko masa yaron ta mika masa .
    “Gsky Muhammed Auwal bashi da kunya ,lokacin da ya
    d’auki yaron sai ya soma murmushi yana cewa “aunty
    muwa kalleshi kiga da wa yayi kama dani ne ko?
    Ummi tace “oho ni yasu wannan yaron na rasa ina
    kasamo wannan rashin kunyar ,oya tashi maza ka bar
    d’akin nan, ‘haba ummi karki min haka mana Dan Allah
    ,ke daya kamata ki tayani dubawa da wa yayi kama
    shine zaki koreni “,ungo nan jairin mara kunya kawai ,da
    ubanka yayi kama ,maza tashi ka fitar min a d’aki
    bunayya ya saki murmushi sannan ya tashi ya fita
    Yana fita yashiga sheidawa abokansa zance haihuwar
    da’akayi masa, yana murna, sannan ya d’aura a duniya,
    saboda jin haihuwar yake tamkar amasa albishiri da
    gidan aljanna.
    ,cikin awa daya kira suka dinga shigowa wayoyinsa da
    sakonni ,duk Wanda ya kira yayi masa barka sai kaji
    yana masawa da ameen ameen ,abunsa har ya daina
    ba wa ummi mamaki
    Da daddare ummi da mai binta mai aiki ,suna zaune a
    parlour’n suna hirarsu ,ita kuwa muwaddat tana d’akinta
    ta tasa jaririnta gaba ta tsura masa idanu tana kallon
    kyautar da Allah yayi mata Wanda ko da wasa bata ta’ba
    tunanin zata iya samun ba
    soyayyar yaron ne ke fixgarta ,ta sauke ajiyar zuciya, ta
    Dan gyara zaman domin kara gyarawa yaronta kwanciya
    ahankali yashigo d’akin ya zauna akan kujera ya kura
    mata ido yana kallonta ‘ke ma kina son baby ko ….?
    Tayi murmushi kawai sannan tace “Ni fa ban iya abinda
    ka iya ba
    Ya matsota sosai yana aika mata da wani tsumammen
    kallo “wani na iya dake baki iya ba?
    ‘ ,duk abinda na iya ,kin iya fiyye dani , dukkanin mu
    muna son baby nan but ki tattara soyayyarki ki ajiye gefe
    saboda nawa yafi naki “tunda Kai ka min na kudar ba ?
    ‘Ko ban Miki nakudar ba ,na tayaki rabi suka dariya .
    Ranar safiyar suna yaro aci suna Ibrahim wanda
    bunayya ne ya zabi sunan,ba’ayi wani abu daya
    danganci bidia ba bunayya ya bukaci a bashi matarsa su
    tare agidan da abi ya gina masa ,amman ummi tace ya
    bari tayi koda kwana arbain ne
    “A daidai wannan lokacin akayi biki al’ameen da faiza
    ,inda amarya ta tare a gidan da dady ya mallakawa
    al’ameen ,faiza dai ta rungumi kaddarar auren a’lameen
    ne kawai ba dan ranta yaso ba,amman asalin soyayyarta
    naga bunayya ,daman kuma haka duniya take ,ba komai
    kake so, kake mallaka ba ,sai abinda Allah ya ga damar
    baka ,Wanda hakan shine mafi alkhari
    Byn shekara biyu
    Ibrahim Wanda ake kira da akram yayi girman ban
    mamaki saboda kulawa da gatan da yake samu agurin
    iyayensa da kakaninsa ,domin wata irin soyayya suke
    nuna masa na fitar hankali inda ummi taso kwarai su bar
    mata shi ,Amman kememe bunayya yaki yarda ,kullun sai
    saka ranar kawo shi yake, Amman yaki har ummi ta
    fahimci bai son basu yaron ne , ta hakura sai dai duk
    weekend din duniya a gidan ummi yakeyinsa…shima Dan
    ya samu damar sakewa da muwaddat ne
    Sosai muwaddat take bawa yaronta kulawa tare da taka
    tsansar aikata wani abu akan idanunsa ,duk da
    kasancewarsa yaro karami bata yarda su aikata wani
    abu akan idanunsa, koda kuwa kiss ne sai bayan
    idanunsa, idan yana gidan ummi kuwa cin karensu suke
    babu babbaka iskanci iri iri bunayya na biye mata
    Mmn sudais ce

    MUWADDAT

    Note
    error: Content is protected !!