Maleeka Malik – Chapter Twenty-nine
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
“”Shigowar Su Malika ne ya dakatar da Saleem daga,d’aga hannun dayayi zai Naushi Bakin Zahra,wacce ta Sulale kasa tana kuka hannunta Rufe da bakinta tana makyarkyarta.
Malika ko Wajen Ayda ta nufa cikin Rawan jiki ta dauketa tana jijjigata batama kai ga Zarafin mgana ba,Taji muryan Saleem cikin wani yanayi yana Fadin”Why..? Zahra me nayi miki..? Me malika ta tsare miki..? Wani alhaKi Yar jaririya Ayda tayi miki da kikeson kasheta.?.”Atare joda da Malika suka kwalolo ido suna bin Zahra da kallo Wacce ke girgiza kai tana kuka take Fadin
“Wlh batamin komai,Sharrin Shedan ne,ammh ni ko kuda Bazan iya kashewa ba..”Tafada tana gunjin kuka tana daga hannuwanta,Saleem bai iya mata mgana ba,sai da Numfashinsa ya koma daidai kafin yace”Hakane bakomai,Allah nagani ban Aureki da Wata Zuciya ba zahra,nayi kokarin ki zama mace tagari hakan ya gagara Daga karshema Saboda bakin kishinki kamaki nayi kina neman kashe yar Jaririyar Allah Wacce bata ji ba bata gani ba,ammh ngode ma Allah daya Toni asirinki Tunkafin ki aikata Abunda kika niyya,kije bazan hada ki da hukuma ba,ammh zan Sallameki daga Rayuwata sallama ta har Abada,Saboda haka kije na Sakeki saki biyu kuma Tsakani dake Zahra Allah ya isa,bazan taba yafe..Miki ba..”Yafada kamar kwalla zata zubomai Shiyasa ya Fice Daga dakin da Sauri yana Share hanci.
Itako Zahra zaman yan bori ta karayi akasa tana kuka hannunta biyu bisa kai tana kururuwa tare da kuka alokaci daya tana Fadin”Wayyo Allah na..!Kaicho na ni Zahra na kashe Aurena dakaina..”Take Fada tana kuka mai hade da Nadama mai karfi,Malika da joda dake tsaye agabanta suka daskare atsaye suna binta da kallon mamaki mai cike da tsoro.
Zahra ta rarrafa zara riko Kafar malika,ita kuma tayi Saurin yin baya tana girgiza kai Wasu hawayen Tsausayin kanta dana Yarta na kamata,kara rumgume Ayda tayi tana Fadin”Ban taba Zaton zafin kishinki akaina har yakai kiyi Tunanin kashe Jaririyar da batasan komai ba,haba Zahra me kika Dauki Duniya ne,duk Abunda Zaman lafiya da hakuri bai baki ba,Wlh tallah akasinsa bazai taba baki ba,Meya Rufe miki ido?Dukiya.?ko ko Shikanshi Mijin..? Wanda duka Zaki Mutu ki barsu anan Duniya kije lahira ki girbi Abunda kika Shuka..,Hakika kin bani mamaki Zahra,ammh kuma ngd ma Allah daya Tsaremin Ayda baki riga kin aiwatar da mugun Nufinki akanta,babu Abunda zence miki,tunda kin riga da knga karshenki..”Tafada tana kuka kafin ta sakai ta Fice daga dakin Zahra na kururuwan Kiran Sunanta.
Joda ta Shiga Tafa hannu tana fadin”Innalillahi ni joda na Shiga Aljannah,ammh dai kinyi Asara wlh,yanzu ke Zahra ina miki kallon mara hankali Ashe kallon biri nake miki kina min na ayaba,Toh Allah ya Shiryeka yasa wannan Ya zameki Darasi knga dai karshen Wanda yaja da ikon Allah don Malika da Saleem haduwar Allah ce bata ta mutum ba..”Tafada kafin tajamata dogon Tsaki ta Fice,
Nan Zahra ta kara Faduwa tana kuka harda birgima Nadama Tare da danasani suka Shigeta lokaci Daya tana Danasanin meyasa ta biyema Sharrin Zuciya Dana Shedan,gashi ya kaita ya baro,yanzu me zatacema iyayenta a auren da ko Shekara bai yi ba..? Bazata iya bude baki ta Furta irin Abubuwan Data aikata Saboda Tasan Halin Abba da momi suma bazasu mata da Wasa Ba.
Gajiya Tayi da kukan ganin babu mafita yasa ta tashi ta Shiga hada kayanta amanyan akwatunanta,Sai da ta hada komai nata kana ta koma ta Zauna tana Sharan kwallah,sai ga Saleem ya Shigo saurin mikewa tayi tana mutseke ido zatayi mgana kenan ya Mikamata Farar Takarda hannunta da jikinta na Rawa ta mika hannu ta karba tana kallon Fuskarshi wanda ya kauda kai alamun bayason ganinta ma kwata kwata,Ta karba ya sakai ya Fice ya barta tana zubewa bisa gado Tana Tsiyayan Hawaye.
Zahra da kanta ta Dinga jidan akwatunta zuwa waje,megadi ne ya Fita ya samo mata mai Napep ta Shiga Zuwa Tasha inda ta hau motar Kano,har suka kai kano Zahra na kukan Nadama da kaicho da Rayuwarta haka Napep din data Shiga da Inda mota ta Sauketa zuwa,gida nan ma kuka tayi tayi,kuma haka ta Fadama Falon gidansu tana wannan kukan megadin gidansu ne ya Shigo da akwatunta yana Sanar da Momi Mai napep na waje yana jiran kudinsa
Momi da ke Falon ita da Nadira suka mike Arazane atare suka Tarbi Zahra suna Tambayanta lafiya bata iya mgana ba illah Takardan da Saleem ya bata ta zaro ta daga cikin karamar jakarta ta mikama Nadira,momi kuma na kokarin ciro kudi cikin pos dinta Dake kan kujeran daya Daga cikin wadanda sukama Falon kwanya 500 ta mikama megadi ammh Rabin Hankalinta naga farar Takardan Da Nadira ke warwarewa tafara karantawa abayyane kamar haka.
_NI *SALEEM KABIR KUMO* Na kara karishe yanke igiya biyun daya Rage a tsakanina da *ZAHRA BUKAR MADA* Sakamakon munanan hallayata wanda in kuka Tambayeta zata Sanar daku da kanta,Ina Rokon Allah in azamana da Zahra na cutar da ita ko na Mintina daya na yarda ku iyayenta ko Rokarmata Allah ya Sakamata,in ko Azamana da ita Ita ta Cutar dani kuyatani Rokon Allah ya sakamin Akanta.._
_* ACP S.K.Kumo.*._
Daga Nadira har Momin hannu Suka Dora bisa kai suna kiran Sunan Allah da Salati lokaci daya,itako Zahra kasa ta Sulale tana gunjin kuka Momi na kallonta cike da Tashin Allah..”Innalillahi Wa’inna alaihiraju’un Zahra garin ya haka ta Faru,yaushe Mijinki ya sakeki da zai ce ya karishe igiya biyun dake Tsakaninku,yaushe wannan Abun ya faru ammh mu bamu sani ba…? Tafada tana Rike haba cike da damuwa,Itako Zahra taki mgana banda kuka babu Abunda takeyi Haushi yakama Momi takai mata Duka tana Fadin”Don Ubanki bazaki mgana ba..? Mekika aikata har ya sakeki saki biyu lokaci daya,kuma a yadda yaron nan yayi Rubutu Zahra kece kika jama kanki Zawarci da yarintarki,Kinje kinyi Abunda kika kashe kanki kika kuma kashe mu iyayenka,Wlh baki kyautamana ba Zahra..”Take Fada tana kuka Nadira ce ta Rikota tana bata hakuri tana Share mata hawaye,itako zahra kukan ta take karama Volume Saboda bata da karfin gwiwa bada lbrin Abunda ya Faru
Momi batayi sanya ba ta Daga waya ta kira Abban Zahra tace ya dawo gida yanzu ba lafiya,jin muryanta cikin wani yanayi yasa ya umarci Direba daya juyo dashi gida,dama yana hanyar Zuwa gidan Wani abokinsa ne,koda yadawo gidan nan ya iske bakin lbri wanda ya kusa saka Zuciyarsa bugawa,yayi tambayan Duniyan nan Zahra taki mgana sai kuka take,daga karshema tashi tayi ta Shige daki Nadira tabi bayanta,ganin haka yasa Abba ya kira Layin Saleem din ammh kuma wayarsa tana kashe,sai ya sauya alaqaan kiran Zuwa ga IGP KABIE KUMO,wanda Shi Abba ne ma ke Sanar dashi Abunda ya Faru don su basu da lbri,ammh yabashi hakuri da janjanta lamarin inda yace zai Nemi Saleem din yaji gaskiyan batu
Abbi Ummi ya sanarmawa Abunda Bukar Mada ya kirasa ya sanar dashi kirji ta Dafe tana salallami,wayar Saleem tayi ta kira bata Shiga sai ta kira na Malika,bayan sun gaisa take Tambayanta ina Saleem,wanda lokacin yana dakinsa duk Wunin yau bai ci abinci ba saboda Damuwa da Nadamar Auren Zahra daya lullubeshi Malika tayi ban hakuri ammh yace ta rabu dashi bayason cin komai,Yana kwance akan gadonsa ta mikamasa wayar tana Sanar dashi Ummi na Son mgana dashi karban wayar yayi ya saka akunne alokaci daya yana gaida Ummi bata tsaya amsawa ba ta Shiga jeromai Tambayoyi kan Abunda Bukar Mada ya kira Abbi ya sanar dashi baiyi Nauyi baki ba ya sanar da Ummi duk Abunda ya Faru baki ta rike tana mamakin Zahra,Duk da Zahra tayi Abunda bai kamata ba,ammh Ummi tanuna Saleem yayi kuskuren yanke Hukunci cikin Fushi,ta kuma bashi Umarnin ya kira Mahaifin Zahra yamai bayani don daga mganarsa Zahra taki mgana,ya sanar da ita zai kirashi da Safe,da haka sukayi sallama tana Fadin Allah ya kyauta na gaba
Koda ta Sanar da Abbi lbrin da Saleem ya bata tsaki yaja yana Sababin Yarinta kenan da Shigen Rawan kai irin na Saleem,ammh ina shi ina mata biyu,da lokacin da ya Rarito an hanashi ba hanuwa zaiyi ba,ammh yanzu wa gari ya waya..? Allah ya kyauta ammh sam basu da Tunani inda suna dashi da duk haka bata Faru ba,shima Allah ya kyautan yayi toh babu wani gyara Tunda Saki ukun ya cika kemata sai Da Fatan Allah yasa yazama darasi garesu gabadayansu…
Hajiya Babba ko dataji Fada takamayi da saleem din wai meyasa bai bata kashin mutuwa ba kafin ya tarata,Shiko Ya marwan dama yace Daga ganin wannan amaryar ta Acp batajin mgama,Saleem ko sai Washegari ya kira Bukar Mada ya Warwaremai zare da abawa Tundaga Farko har karshe sai gashi Daga karshe Bukar Mada kebama Saleem Hakuri yace babu komai kanta tamawa,koda Hajiya Saratu momi taji batayi wani mamaki ba,don tasan wauta da sakarci irin na Zahra kuma ga Abunda Nadira tace ta kirata tana fada mata,duka Momi ta hada Fadan da kuma Takaichin Zahra ta Watsar illah ta Sanar da ita idai kan kishiya zata kare rayuwarta aiko Tana da Wahala don yanzu Rayuwa ta chanza ba lalle bane mazan yanzu su zauna dakai kai kadai ba,balle keda kika je kika tarar ammh har kina da kokarin Son ki kori ta ciki,wanna Shine kaikayi ya koma kan mashekiya.
*
Sai bayan kwana biyu kana Saleem ya warware,ranar monday ya Fita office,ammh adaren sunyi Tsiya da Malika kan tacemai ita daya nemi Shawaranta da bai saki Zahra ba,Wanman mganar Shiya batama Saleem Rai har ya Nunama Malika hakan,Dakyar ta bashi hakuri ya hakura ammh ada har ya dau Zafin da Cewa kila ko bata Sonshi ne,da har zata ce ya cigaba da zama da Zahra wacce bata son Jininsa toh aiko bata Sonshi karyan banza ne kawai.
Da Maman Abba Taji lbri sai da tayi Guda bayan ta juya Duwawau Tacema Malika ta tayata barka,domin Rabuwa da muguwar kishiya irin Zahra babban nasara ce,wanda zama dasu bala’i ne Tunda Zuciyarsu bata da kyau sam,Toh ita kanta Malika Tasan Zahra ba masoyiyarta bace,ammh sakin ne bai mata dadi ba,shiyasa ko da taga Saleem yasa anfitar da komai dake dakin Zahra an saka Sabbi tsoffin kuma yabama megadi yace yakai ma ilayanshi ya karba yana murna Hade da godiya,Sai merry ta koma tana kwana adakin,joda kuma bata dade ba takoma Katsina wajen Hajiya.
*
Yanzu gida ya rage daga Malika sai mijinta Saleem sabuwar Soyayyah mai dauke da Sabuwar Rayuwa mai cike da muradi da burgewa nan suka bajema juna yadda suke kaunar junansu,kowa yana kafa kafa da Dan’uwanshi bayason bacin Ransa,gefe daya kuma suna kula da yarsu Ayda wacce take kiba tana kuma kara girma da Wayau,gefe daya kuma Malika na ta Shiryen Shiryen Biki wanda Abun ya Hade mata gata wan mijinta ne,Gata kanwar amarya kuma kawa gareta,gata kuma ta wani bangaren tamkar Uwa take gareta Tunda komai na Shiryen Shiryen bikin Hajiya Binta ita ta sakarmawa Shiyasa koda yaushe cikin mgana Suke awaya don ganin yadda Abubuwan zasu tafi kan Tsari.
MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
