Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
    “”Saleem sai washegari da Safe yazo,inda aka hadu aka Raba gadon Tarin Dukiyar Daddy,wanda Malika ta samu kaso mafi rinjaye da tsoka domin kusan rabi da kwatan Dukiyar natane,Hajiya ma ta samu nata kason,Sakamakon Dady bashi da uwa ba Uba,kuma ba wani dan’uwa da suke Daki daya ko kuma yan Uba duka Babu wanda zai iya gadanshi bayan Malika da hajiya,sai kuma cikin kawunan Daddy akwai wadanda suka Shigo cikin magada.

    Anan Hajiya take Sanar da Malika cewa Zata koma Malumfashi ita Joda,tunda gidan da suke ciki malika ta gajeshi,ai nan da nan Malika tace batasan wannan Zencen ba,Tace Har Abada hajiya bazata bar gidan ba,zata cigaba da zama tare dasu merry ita zata cigaba da biyansu,kana manajojin Kamfanonin Malika tayi mgana dasu Tace su Cigaba da gudanar da komai sai lokaci bayan lokaci zasu dinga mgana ta waya,hannayen Jarin Daddy na kasashen ketare kuwa an Dawo dasu ne an rabasu,tsabar kudin da Malika ta mallaka banda kamfanoni bata san iyaka ba,shiyasa kuma bada cigiyar Filaye inda tace tana so agina islamiya,da masallaci,domin sadakatul jariya zuwa ga Daddy.

    Hakika wannan bayanin nata ta saka Farinciki azuciyar kowa,mussaman Mijinta Saleem wanda Farincikinsa yakasa boyuwa har sai da ya bayyana mata,bai koma Zamfara ba aranar sai awashegari ammh yammah nayi yace Malika ta Shirya tazo suje yawon bude ido😂Tako cakare ita da Ayda Suna Fita bai su zame ko’ina ba sai gidansu wanda Daddy ya basu,Allah sarki megadi na nan da wani wanda yake kula da gidan,komai yana nan amuhallinsa babu Abunda ya chanza.

    Malika tasha mamakin ganin hatta cikin dakunan tsaf tsaf,ashe Hajiya ta kansa merry da Dose suzo su gyara lokaci bayan lokaci,basuyi masauki ako’ina ba,sai akan gadon Da Saleem ya karbi budurcin Malika haka ya Rumgumeta kam idanuwansa alumshe yake Tambayanta..”Kin Tuna wannan gadon Ummu Ayda..”Cikin kasala ta dagamai kai bai bata zarafin mgana yace”Toh wannan gadon shi yakafa miki tarihin zama azuciyata wanda baki Fita ba,kuma bazaki Fita ba har Duniya ta tashi..”Kuramai ido tayi cike da mamaki tana kallonshi bai bata xarafin mgana ba,sai da ya tsotse lebunanta kafin ya hada dogayen hamcinsu waje daya yana Fadin’Tun Ranar dana aikata miki wannan Abun,ban kara Sukuni ba,tunda lokacin Ashe sonki ya Shigeni sai nake dauka Tsausayinki nakeji sai daga baya na Fahimci na Fada acikin kogin sonki wanda baida iyaka,Wlh Malika zuciyata tanayin Xafi matukar na ganki cikin damuwa,kukanki tamkar zubowar dalma daga zuciyata,Bata miki rai kuwa tamkar Nima an batamin ne,Bana samun sukunin zuciyata sai naji gangar jikina ta hadu danaki..Yau na Na sanar dake Abunda na boye miki I SO MUCH LOVE U MALIKA…”Ya Fadamata idanuwansa na chanza launi.

    Kamkameshi Malika tayi tana hawaye Da dariya lokaci daya,Kanta takara tusawa bisa kirjinsa tana Fadin”Bani da bakin mika godiyata gareka,domin asanadin Abun ka min akan gadon nan,ya chanza rayuwata na dawo malika datace na dawo mace kamar kowa,har Abada kai Abun alfahari na ne,Duk Abunda kamin bai hana zuciyata ta Fada tarkon sonka,Ina Sonka Abbu Ayda fiye da Yadda nakeson kaina..”Tafada tana dago kanshi bakinta takai kan nashi Tafara tsotsan lebenshi cike da kwarewa shima kan nata ya rike da hannu bibbiyu ya mikamata harshensshi tana cigaba da Kissing dinshi kamar Allah ya aikota shiko gabadaya jikinsa da hannuwanshi rawa suke saboda yadda Malika ke Tafiyarshi dashi cikin Kwarewa.

    Ayda ko na gefe tana barci,iyayenta ko sun gama rikita juna,cikin xafi zafi Suka raba kansu da kayan jikinsu suna kara Shafa sassan jikin junasu cike da So da kauna,Awannan daren Darene mai cike da tarihi wanda Malika da Saleem bazasu manta dashi ba,darene daya kunshi tarihi kala kala,sun gudanar da wata rayuwa mai tsayawa azuciyr masoya,haka Saleem ya kwana yana jadaddama Malika kalmar yana Sonta,tagani kuma ta yaba domin ya nunamata a aikace haka Saleem ya tasata lasheta daga sama har kasa,itakuwa ta jiyar dashi madaran dadin daya Kasa controlling kanshi tasha Surutai sai da tagaji Ta rufemai baki.

    Washegari da Safe tare sukayi wanka su kama Yarsu Ayda kowannensu anan ya chanza kaya Tunda dama Daddy ya siyasu komai,kamar karsu bar gidan haka suke ji,shiyasa Saleem yace zai nemi Transfer adawo dashi Katsina sai su tararra su dawo nan,Malika ko taji dadin haka sosai,sai da suka koma gida yayi Sallama dasu hajiya kana ya Sallame Malika kafin yakama hanyar komawa Zamfara cike da kewar matarsa da soyayyar yarsa Ayda..

    *

    Zahra yanzu ta Sadda kai kasa ne,in kuka ga yadda takema Saleem ladabi da biyayyah sai kun yi mamaki baya mgana kanta na sama sai akasa,kuma kullum cikin makircin tambayanshi take yaushe malika zata dawo..? Tayi kewaar Ayda sosai,sai da yayi mirmishin jin dadin Zahra ta zama mutum yace Suna tafe insha Allah.

    Ganin haka yasa Saleem ya sakarma Sosai suna baje Soyayyarsu domin Ta nuna itama tana kaunar Malika da Abunda ta haifa baisan ta munafuncin bane,gashi taci riba domin Saleem yanzu yana kokarin bata lokacinsa sosai suna shan love wanda ko lokacin amarcinsu basu sake da juna haka ba.

    Malika ko sati daya tayi A katsina ta Wuce Malumfashi tayi kwana uku wanda babu Shakka dangin mahaifinta sukaji dadin ganinta ta zaga dangin sosai wanda dama tare da Joda sukaje,dagachan suka Wuce Abuja,Ummi da Abbi kamar su goyata haka suka dinga dawainiya dasu,Ayda ko suna zuwa Abbi ya amsheta suna sama wajensa,Saboda dadin zama agidan Ummi sati daya cur Malika ta kwashe,ada har tana da niyyar karawa Saleem ya kirata awaya yace in takara bada yawunshi ba ta dawo don wlh ya gaji kewarshi zata illatashi,Aiko da Ummi sukaji zata koma aiko tace batasan wannan Zencen ba,sai taje kumo ta dawo kafin ta koma,Ransa baiyi dadi ba da Ummi ta kirashi tana Sanar dashi sai Malika taje kumo ta dawo kana,bashi da yarda zaiyi dole ya hakuri suka tattara suka Tafi kumo duka gidan harda Hajiya,kwana daya sukayi suka dawo Ita kanta Malikan kwana Daya ta kara Direba ya kwasheta ita da Merry Tunda Joda Tun a malumfashi ta barta,shiyasa hajiya tace tazo da merry saboda ta dinga taimakamata da Renon Ayda in ita kuma tana wasu ayyukan,ammh sai da ta kira Saleem ta nemi izininshi baiyi gaddama ba ya amince,Malika bata yi kasa agwiwa ba tazo da System dinta wanda rabin kasuwancin mahafinta keciki,tazo dashi saboda tana so ta Tuntubi Saleem in zai barta ta dinga gudanar da komai tana gida basai taje ba,Tund Gabadaya babu Abunda bata sani akan kasuwancin ba.

    Saukan yammah sukayi so Saleem baya gida sai Zahra wacce tayi kiba kamar ba ita ba,tadai Fito tayi musu sannu da zuwa daganan tayi komawarta daki Ranta bakikirin Da dawowar Malika wanda ta sani yanzu duk Jin dadin data samu zai rage ne,haka ko akayi don Ranar ko takanta ma Saleem bai bi Tunda ya dawo yana nanike da Malika,Tunda suka Shige daki basu Fito ba Sai Washegari wanda hakan ya kona ma Zahra rai kamar tayi Bindiga saboda kishin Malika balle yanzu dataga tafi da kyau da iya tsara kwalliya komai na Malika mai kyau shiyasa komai ta saka yake mata kyau,bata kwalliya sosai ammh kuma duk kayan data sanya sai sun amsheta,balle Ranar girkinta yazo bata wasa da duk Abunda ya Shafi mijinta,Komai zatayi sa cikin lokaci ne,bangaren girki kuwa Malika bata da mtsala domin ko gane wani Abu ne batayi ba,zata dauki wayarta tayi browsing taga yadda komai yake ta kuma yishi yadda yakamata..

    Zumuncinsu da Maman Abba ko yakara kullewa ita ke kara koyamata wasu dabarun zama da miji ammh ita malika Tuni ta samu key din Rayuwar Saleem ahannunshi,Bata mai gaddama kan Abunda ya haneta,koda tana son Abun nan da Zarar yace “A’a to ta barshi har gaban Abada,kuma ko Fuska bazata nuna taji haushi ba,Abu na Biyu bata Raina Abunda yake mata ita da yarta komiye in ya Siyo mata zata karba ta Gode masa sosai yadda kasan ba’a taba mata makamanciyar kyauta irinta ba,Duk da ko tarin Dukiyar da Allah yayi mata bata Raina Abunda mijinta yayi mata,sai Abu na uku Tarbiya Malika bata tsalleki mganarsa tana girmamashi tare da ganin Darajarsa in yace ga hanya tabi nan take saka kai babu gardama gata da Sanin wayewar Duniyar Tafiyar da miji cikin sauki,toh tana da iliminta daidai Gwargwardo to wadannan hallayar ta Kara sace Zuciyar Saleem wanda ko mgana tayi Shima bai iya tsallaketa,kuma yake Fifitata akan kowa duk da yana kokarin kwatatan Adalci Atsakaninsu da Zahra,ammh bata ganin kullum cikin kishi take da kyashi akan Malika da yarta..

    Mganar kula da kamfafoninta da suka zama mallakinta kuwa Tun kafin tayimai mganar ya Tuntubeta ya kuma bata dama ta rika gudanar da Komai acikin gida,Tunda ga Na’ura mai kwakwalwa ga waya,Shima yayi mata alqawarin bata dukkan gudummuwanshi Murna wajen Malika ba”a mgana dama ita tana son kasuwanci sosai nan da nan ko tacigaba daga inda ta tsaya rabonta da wani Kamfanin daddyta Tun kafin Aurenta da Saleem,yanzu kuma saboda karfin gwiwanshi da Soyayyarshi gareta ta fara Dawowa Ainihin Malika malik dinta,ammh wannan ba Wacce kuka sani abaya bane,ta yanzu She very smart and Educated both na addini dana boko.

    Sai ya koma in tana kan Na’ura Merry ke kula da Ayda,ko in tana kichen tana girki Ranar ko da bata da aiki Shikenan ammh merry ta taimakamata sosai Duk da ma Aydan bata da Rigima sosai,Abu daya Fara Tunzura Zahra Shine Soyayyar da Saleem ya kwashe kaso mai yawa yamikama Ayda wanda ko ita matarsa baya Sonta haka,Ko malika kedashi ko ita kedashi yana Nanike da Shegiyar yarinyarnan baya ijiyeta sai dare ya tsala lokacin kwalliyar datayimai Duk tagama goge kanta Saboda Haushi ma tafiyarta dakinta take tayi kwanciyarta sai sanda yagaji da kanshi ya maidama uwarta kana zai zo ya kwanta,wani zubin har ta Fita girki baya Nemanta Saboda daya dawo bashi da Hutu jikinsa na Rawa zai karbeta da ita zaici abinci wanka ne kadai ya ijiyeta in zai Shiga,wannan Abun yanzu Shike damun Zahra sai ma tatarra tsanarta kacokan kan Ayda wacce batafi wata uku Aduniya ba,in ko ya ijiyeta ya Shiga wanka haka Zahra zata dinga Dungurin yarinyar tana hararanta sai taji motsin zai Fito sai ta dauketa tana lallashi kamar gaske,shiko ganin haka sai yaji dadi har yana cemata in taga Malika na aiki ta rinka zuwa tana daukan yafi merry wacce ba musulma ta dinga wahala da ita,sai ta nuna kamar ta Allah harda cemin tana matukar Son Ayda kamar Ranta,shiko har Ga Zuciyarsa yace mata tabari Malika ta sake haihuwa sai su bata,Wani bakin ciki ya cika mata rai wato Malika ne zai karama ciki ta haihu ba ita ba ko? Tundaga lokacin ta dauki damaarar Azabtar da Ayda matukar ta Shigo hannunta,musamman take karbanta ahannun merry ta Shigo da ita daki ta dinga saka yarinya kuka tana mganarinta tana zaginta,sai gaji da kuka zata maidama Merry ita kuma ta kaima Malika ta bata nono,Wanda zatayi ta mamakin ganin Ayda haka duk tasha kuka Fuskarta tayi jajir,ita da bata da Rigima ko ta tambayi merry sai tace Anty Zahra ce ta karbeta,jin haka yasa Malika bata Shigo da wani Tunani zatayi Saurin kauda Shedan daga Zuciyarta.

    *
    Bayan Sati biyu Zahra ta samu waya daga kano cewa An kwantar da momi Hajiya Saratu a asibiti,Dole suka Shirya tafiya harda Malika sukaje suka dubata,ammh su sai ka dawo Saleem yace Zahra ta zauna ta kwana biyu Tunda dama bata taba zuwa ba,ammh afuskar Zahra ya Fahimci bata ji dadin Cewar da yayi zai barta ba,haka ta bata rai har suka Tafi,ita kuma ba komai ne yamata bakinciki ba,sai yadda zata bar Malika da mijinta su kadai agida shine kishi ya Turniketa taji kanon ya Fita aranta,itako la’akari da Momi dake kwance ba lafiya batayi ba,A’a ita hankalinta na gida,Shiyasa Adaddafe tayi kwana hudu ta dawo sai dai suka ganta kwatsam,Saleem yayi mamaki Domin Sati daya yace tayi daya tambaayeta ba’asi sai tace Ai momin ce taji sauki Ita tacema ta taho gidan Mijinta,alhalin ko achan cema Momi tayi ita da Nadira Cewa Saleem ne yace kwana uku yabata ta dawo gida,Abba najin haka ya hadota da Direba ya maidota Zamfara.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!