Maleeka Malik – Chapter Seventeen
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
………….Rumgumeta hajiya tayi tana Fadin”Kai Saleemata,sannu da zuwa…”
Saleema na dariya tace”Yauwa hajiya,ya gida..? Kewar gida ya dameni sai kuma muka samu dan break shine na taho gida..”
Kafadanta ta dafa tana Fadin”Muna munsha kewarki sosai ma kuwa..”Mirmishi tayi mata tana mikewa daidai lokacin da suka sake hada ido da Malika,wacce tun kallon da Saleema tayi mata taji ta muzanta,Sai ta koma gefe ta rabe,kanta duke ta kurama littafin gabanta ido,kamar tana karatu nan ko, ba karatun take ba,Jikinta duk asanyaye.
Ganin sun kara hada ido ne yasa Malika tace ma Saleema”Ina yini,sannu da zuwa..”Wani dirty look Saleema ta watsa mata kafin kawai ta dauke kai,don ta Shaida ta tantiriyar matar Ya saleem ce,domin Abbi ya sanar da Ya marwan duk Abunda ya Faru,shiko ya sanar ma da gindin rasit,wato Sadiq,shikuma ya sanarma patner dinshi Saleema,wacce kwata kwata Abun bai mata dadi ba,ita fa bata ga dalilin Abbi na takurama ya saleem kan wata chan banza jinin arna ba.
Ganin yadda tayi mata ne,yasa malika taji idanuwanta sun kawo, ruwa Hajiya ce taga Abunda ya Faru ranta bai mata dadi ba,ta kalli Saleema tana Fadin”Saleema bakiji Matar yayanki na miki sannu da zuwa bane..? Tabe baki tayi tana jan akwatunta take Fadin”Wace…? ta fada tana dan kallonta cike da raini.
Ganin haka yasa Hajiya mika mata dakuwa tana Fadin”Uwarki ce..”Baki ta tura kafin tayi gaba tana Fadin”Au kefa hajiya,baki ma mutun kawaichin marmari wlh..”Tafada ranta bace,ganin an zageta kan wata banza.
Da Ummi taci karo ta Fito daga kichen,Rumgumeta tayi tana Fadin”I miss u my Ummi..”Shafa kumatunta Ummi tayi tana Fadin”Likita na wasa da karatunta ko? baki da aiki sai tahowa gida..”Dan dira kafa tafarayi tana Fadin”Kai Ummi break fa muka samu na one week,kuma nayi kewaeku ne,shiyasa nazo ganinku..”Sakinta Ummi tayi tana Fadin”naga alama,toh baki tsayawa chan kiyi karatu? .
Tura baki tayi tana Fadin”,Kai Ummi,ga kayan karatuna na nan cike da jaka,..”Dariya Ummi tayi mata tana Fadin”Uwar zence,kinganki Saleema bamai kadake azence..”,Itama dariyan ta kyalkalyalace dash tana Nufar hanyan dakinta tana Fadin”Kai Ummi,me kike dafa na mana ne..?
Shiga kigani..”Ummi ta bata amsa,Yar dariya tayi tana Fadin”Wai ni banga Abbi ba,kuma banga Malalacin Acp ba..? Tsaki Ummi taja tana Fadin”ke wai bana rabaki da sha”anin saleem bako.? Sun fita shida Abbi..”Dariya Saleema tayi tana
Fadin”Kai Ummi bafa ni na sakamai sunan ba hajiya ce gatan chan..”Tafada tana nuna hajiya.
Hajiya ko datake da cikinta na Abunda tayima malika,kyabe baki tayi tana Fadin”Kwarai ni na samai sunan,ammh sai na kirasa ya amsa don dole,kuma koda yaji haushi ban dakuwa,ke kuwa wlh kika kirasa da wannan sunan dakaina zan umarceshi daya nada miki na jaki Tunda baki da mutumci..”Tafada tana kumfar baki,Bude baki Saleema tayi kafin ta kada ta Wuce dakinta tana Fadin”Tabdijam,gamdamemiyar budurwan,da sake kam..”Tafada tana Shigewa dakinta dake yammah da na hajiya.
Malika ko na jinsu duk Abunda ke Faruwa ammh kanta na duke takasa dago kanta,Hajiya ce ta kira sunanta tana Fadin”Malika kiyi hakuri kinji ko? ahankali zaku saba da ita,ita kebima saleem..”Mirmishin yake tayima Hajiya tana Fadin “Babu komai..”Tafada tana kokarin maida hawayenta,kara sunkuyar dakai tayi tana Tunanin rayuwarta abaya ta tabbata da adane da kudi aka hada Saleema akace tayi mata Abunda tayi mata bazata taba yi ba,ke ko kusa da ita wlh bazata iya zuwa ba,ammh gashi yanayin rayuwa ya chanza da ita,har ana mata duk cin kashin da”aka ga dama Ammh babu komai tayi niyyar Tuba ga Allah kuma bazata koma ga halayyyata ta baya ba.
Tashi tayi ta tatarra littafanta takoma daki ta kwanta bisa gado tana kuka,saboda takasa rike zuciyarta waje daya tsausayin kanta duk ya lullubeta,sai da tayi kuka ya isheta kafin ta mike ta fada tiolet ta dauro alwala tazo tayi sallar azahar,Bata son sake Fita taje su hadu da Saleema ta kara Wulakanta ta,shiyasa tayi zamanta adaki tana cigaba da duba littafanta,.
Har akayi sallar mangariba Bata fito ba,sai da Ummi taji ta Shuru ne ta Shigo har dakin ta isketa saman darduma tana duba karatunta,Har ga Allah Abun Nama Ummi dadi ganin yadda malika take maida hankali wajen koyon ilimin addini,Gefen gadon ta zauna tana Fadin”Dota Anata karatun ne..? Gyada mata kai tayi tana Fadin”Eh Ummi sannu da aiki..”amsa mata tayi da kai tana Fadin”Yayi kyau in kingama ki Fito Falo,yau mu taru muyi Dinner kinji..”Gyada mata kai tayi kafin tace”Toh Ummi..”Tashi tayi ta Fice ta barta nan tana cigaba da karatunta.
Koda Malika ta Fito babu kowa cikin Falon sai Ummi dake kwaso kololin abinci ,tana ganin haka ta isa gareta Da Sauri tana Fadin”Sannu da aiki Ummi..”
Tafada tana karban kololin ahannunta,sakarmata Ummi tayi tana Fadin”In kin kai wannan maza kije ki zauna kinga baki da lafiya kinji ko? mirmishi kawai tayi tana Fadin”La wlh Ummi naji sauki bakima gani Ba..”Tafada suna karisawa bisa Dinining din,duk yadda Ummi taso tahana Malika kin hanuwa tayi,tare suka Jera komai,sai alokacin Saleema ta Fito daga daki,cikin riga da sikat,Wayace ahannunta tana latsawa kallo daya tayima su Ummi da malika ta dauke tana tabe baki
Ummi ce tace”Sarkin waya,sai yanzu kika Fito na shiga naga kina wayarki na fama..”Ashagwabe Saleema tace”Kai Ummi,ni fa da ya sadiq ne..”Tafada tana zama bisa daya daga cikin kujerun Falon,tana dariya,Kafin Ummi tayi mgana sai gaAbbi yayi sallama yana sawo kai falon,bayanshi kuma Saleem ne yana sanye da wata danyar gezner Light blue,wacce taji kyau dinkin muhammed,da hulansa zanna bukar,kayan su matukar amsanshi fuskarshi babu alamar fara”a ko kadan,sai dai bai tamketa sosai ba.
Da Gudu Saleema tatafi gareshi ta fadamai tana mai sannu da zuwa,Riketa yayi yana tambayanta yaushe ta dawo,tace dazu ba dadewa Saleem dake bayan Abbi hankalinshi na bisa waya yaji saleema ta fadomai tana fadin”Mai girma Acp.”Ta fada tana Rumgumosa.
Wayarsa ya maida aljihun yakama kunnan Saleema ya murde yana Fadin”Ke wai bakison karatu ko? baki da aiki sai guduwa gida,Allah sa wannan Semister akori wlh..”tanajin haka ta sakeshi tayi baya tana diddira kafa sai kuka tana Fadin”Wlh Ta Allah bataka ba,Abbi kaga ya saleem ko? wai za”a koreni daga faculty mu..?
Abbi dake zama bisa daya daga kujerun falon,yake fadin”Tunda har shi yagama ba”a koreshi ba kema haka zaki gama insha Allahu..”Dariya takama saleem yadan dara yana kallon Saleema yana mata gwalo,Ummi ce ta kariso wajen ita da Malika wacce ke satan kallon Saleem,shiko ko barayin datake bai kallah ba.
Sannu da zuwa Ummi tayima Abbi kafin Malika ta duka tana gaisheshi,cike da kulawa Abbi ya kalleta yana fadin”Malika,ya jikin ki? ya bakunta,hop dai babu wata damuwa ko?Girgiza kai tayi kanta na batace komai ba,Abbi yace”Toh masha Allahu,Allah kara lafiya,komai dai kike bukata,ki sanar da Umminku gatanan kinji ko”Wannan karon ne ta bude baki tana Fadin”,Tom Abbi nagde sosai..”
Mikewa Abbi yayi yana tafiya zuwa sama yake cema Ummi “Wai ina hajiya banji duriyanta ba..? Saleema tayi karaf tace”Hajiya yau fa adame take,sai Fada take da mutane,hardani yau ban tsira ba..”Karamin tsaki Saleem yaja yana fadin”Wa.? ai wannan hajiyar ta Abbi ko ba”a mata komai kullim cikin Fada take,ita ko gajiya batayi.”Abbi yawuce kawai baice komai ba saima mirmish dayakeyi.,Ummi tabi bayanshi tana ma su Saleem dariya da Fadin”Ku shiga hankalinku,wlh in tajiku yau ko Sarkin kumo bai isa ya kwace ku ba..”
Falon ya rage daga Saleema sai Saleem da Malika,wacce ke gefe zaune arakube kanta duke,hanyar dakinsa yabi Saleem ta kirashi tana fadin”Ya saleem..”Waigowa yayi yana Fadin”Miye..? Yamutsa fuska Tayi tana kallon barayin da Malika take tana fadin”Ashe kuma Abbi ya matsa maka sai da kadawo da wannan watsatsiyan yarinyar gaskiya ban…”Kallon da Saleem ke watsamatane yasa tayi Shuru ta bakinta tana binshi da kallon mamaki
Ransa kawai yaji ya baci da Saleema tacema Malika watsatsiya,ko banza shine shaidan Malika,domin shi ya fara saninta abudurwa,ko bakomai zai kareta saboda martabanta,barayin malika ya kallah,suka ko hada ido,idanuwnta cike da kwallah har suka zubo,tayi saurin sadda kanta kasa tana share kwallah,sai yaji zuciyarsa batayi dadi ba sam,.
Hade rai yayi yana kallon Saleema yace”inji uban wa yace miki matata watsatsiya ce? Saleema wai yaushema kika rainani,am your mate dazaki tareni da wannan banzar mganar..? Ya fada yana kafeta da rikatattun idanuwanshi,Tura baki tayi tana fadin”Daga mgana sai cibi yazama kari..”Tafada tana juyawa zata koma daki,cike da Fushi yace”Saleema…!..
Ya kirata da karfi,cak ta tsaya kafin ta waigo tana kallonshi Hannunsa ya tura ciikin aljihun wandonsa yana Fadin”Maza go and tell her srry,yanzunan if kuma..? Yafada yana Kuramata ido,Saleema tayi tsuru tana raba ido,tanajin aranta wannan ai reni ne,ganin tana turamai baki ne yasa yafara takawa zuwa gareta yana fadin”Wlh in baki bata hakuri ba, sai na ci ubanki yanzu nan na tatttakaki awajen nan,kuma na hadaki da Abbi,stupit gal kawai..”,Wani kunya Saleema taji da takaichi kamar tayi kwallah,jan kafanta tayi zuwa gaban malika tana fadin”Srry…”Kanta gefe tafada,Malika dake duke ta dago tana mirmishin yake,tace”Bakomai..”Tafada tana jin kamar ta rushe da kuka.
Wani banzan kallon ya watsama Saleema yana fadin”Get away from here,and dis is d last zaki kalleta ki cimata zarafi in kuma baki ji ba,try me and see..”Yafada yana kada mata hannu,kuka yazoma Saleema ta kwasa da gudu zuwa daki tana kuka tsaki yaja yana Fadin”Munafuka kawai..Yafada yana juyawa zuwa dakinsa ransa amatukar bace.
Bayansa malika tabi da kallo tana jin wani iri aranta,Akwana biyun da sukayi tare,in tace bata shaku dashi ba toh tayi katuwar karya haka kurum takejin sha’awar kallonsa,sannan muryansa tana jefata cikin wani yanayi wanda takasa fassarashi.
Tashi tayi tabi bayanshi zuwa cikin dakin,sai ta iskeshi yana Kokarin tada sallar isha”i,batayi sanya ba ta Fada tiolet ta dauro alwala tazo da hanzari tabi bayanshi yajasu sallar,suna idarwa tace mai zata biya karatunta,bai musa mata ba,tabiya shi ko tar babu gardama,Karamata da sura biyu yayi zuwa gobe,tunda yaga karatun nata yana sauri sosai,Ummi ce ta kirashi awaya tace su Fito Falo suyi Dinner,bai sanar da ita ba illah Ficewa da yayi yana Fadin”Ki zo Ummi na kira..”
Hijabinta ta dauka,wanda tazo dashi don dai bata da wani,Koda ta fito duka iyalan gidan sun hallara bisa katon tibirin cin abinci,hajiya babba ce kadai bata awajen,may yau bata ra”ayin ci tare dasu ne,don yau kam hajiya tsiya takeji,Saleema na kusa da Ummi,inda Abbi ke gefenta sai Saleem dake gefen Saleema,Jikinta asanyaye ta karisa tunkafin taja kujera Ummi tace”,Saleema gyarama Antynki inda zata zauna..”
Wani takaichi ne ya kule dama bata Wuce da Abun da ya saleem yayi mata,Shiko yana cin abincinsa ko kallonta ma baiyi ba,balle ya lura datana jin haushinsa,Dkyar taja mata kujeran tana sakin wani Siririn tsaki,Zama malika tayi tana dan mirmishi kadan,Ummi dakanta tayi sarving dinta Tuwon Shinkafa ne miyar agun,wanda yaji manshanu da naman kan rago,Tun kafin ta fara ci taji miyanta ya tsinke,cikin Son cin tuwo taja cokali tafara ci,itako saleema na gefe tana Faman zabgamata harara,wanda data dago ido,Zata ganta tana mata wani kallo,sai dai ta maida kanta kasa kawai idanuwanta su ciko da hawaye,saboda ita bata saba da wannan rayuwar ba.
Saleem yana gama cin abinci ya yagi tissue ya goge baki yana Fadin”Abbi gobe fa zan koma bakin aikina..”Abbi yana cin abinci ya ijiye yana Fadin”Masha Allah,har kun gama mana bakunci zaku tafi? Toh Allah kaimu..”Jin Abunda Abbi yace ne yasa yace”A”a Abbi nikadai zan koma,ai Ita tana nan tare daku..”
Zuramai ido Abbi yayi yana Fadin”Miye dalili..? Kai tsaye yace”Toh Abbi nake ga kamar hakan shine daidai..”Ajiyar zuciya Abbi yayi kafin yace”Ko daya sai dai kace kai hakan ka tsara,toh don mai garinku in katafi ka barta anan wajen wa zaka kabarta..?”Wani miyan takaichi Saleem ya hadiye yana Fadin”Tare daku mana Abbi,kofa na koma kasani ba zama nake ba,toh sai naga data rinka zama ita kadai gwara na barta nan ko banza zata dinga ganin mutane..”
Mirmishin su na manya Abbi yayi kafin yace”Ra”ayinka kenan Saleem,ammh ba gaskiya bane duk uzurin daka bayar bamasu mihimmaci bane mallam,ka dauki matarka kawuce wajen aikin ka da ita,kana da muhallin bawai baka dashi bane,….”,Saleem yayi jagale yana jin wani takaichi kamar ya fasa ihu,
ya bude baki zaiyi mganan kenan Abbi ya dakatar dashi da cewa”Kul..Karka kara cewa komai,ka dauki matarka ku tafi,fakat umarni ne ba shawara ba..”,Yana gama fadin haka ya mike ya haye sama,Malika dake zaune jikinta duk yayi sanyi ganin yadda Saleem din yayi,ada in akace tabishi bazata ba,ammh ayanzu batason ya barta anan,saboda shine gatanta duniya da lahira kuma bazata so ya barta da saleema ba,don sai ta zaneta saboda yadda take wurgamata wani banzan kallo
Ummi ce tace”Ai kaji Abunda Abbinku yace ko? bai samu zarafin mgana ba ya daga mata kai,maida kallonta tayi kan Malika tana fadin”Dota kina so kibishi..? dagowa tayi tana kallon Ummi,kafin ta maida kallonta kan Saleem wanda ya kafeta da ido yana kallonta cikin wani yana so yaji mezata ce,itako wani yanayi taji yana shiganta saboda yadda ya tsareta da manyan idanuwansa masu dauke da wasu surrika
kanta ta dukar kafin ta gyadama Ummi kai,washe baki tayi tana Fadin”Masha Allah,tashi to kije ki Shirya kayanki,Da safe zaku wuce ko Saleem? Gyada mata kai yayi,yana mikewa bai kai da gama tashi ba Saleema ta ture kujera tana sakin wani wawan tsaki takama hanyar dakinta tana kunkuni,dukkansu da kallon suka bita na mamaki,Saleem ne kadai da malika su ka san dalilinta na yin gaba,Ummi ko ta dauka ko wani ne ya bata mata rai.
Adan kaikaice yabi bayan Saleem da kallo,Ransa ya baci da Abunda Saleema tayi mishi,yanzu ko bashi ba,ko malika ai ba sa”arta bace kuma a al”adance tana mtsayin Antintane,ammh saboda ta rainashi shi takema tsaki,Tunda ni sa”anta ne,bai yi yunkura binta ba ya kada kai yabi hanyar dakinshi yana cije baki.
Malika bata bi bayanshi ba,sai da taya Ummi suka maida Kayan da suka bata zuwa kichen,Ummi taso ta hana Malika wanke wanke,ammh taki,tace sai tayi hakan ta barta suka wanke tare,sunayi suna hira,Ummi na kara mata nasihan hakuri da rayuwa,da kuma hakuri da biyayyah da mijinta,sannan Ummi ta roketa alfarma kada bayan sun koma zamfara ta yada karatun data fara koya,tace zata sanar da Saleem yasata a mkranta islamiya na matan aure,wanda zai taimakamata sosai..
Hakika taji dadin Nasihan Ummi da shawaranta,ita kuma tayi mata alqawari zata sameta mai Bin umarninta,Ummi ma taji dadi tayi ta sakamata albarka,wanda Malika taji dadi harda kwallah,saboda Farinciki don bata taba samun saka albarka daga wani ba,bayan Daddynta,sai gashi Ummi na sakamata haka Abbi,ai ita babu Abunda zatace da Ahalin Kabir kumo,sai godiya da Fatan alheri.
Koda ta koma dakin ta iske Saleem kwance ya juya baya yana kallon bango,wayarsa kuma sai daukan Tsuwa take,ammh sai ya dinga saka hannun yana latsewa,ganin bai mata mgana ba yasa ta fada tiolet ta wanke baki kafin Ta fito,wajen akwatun nanta ta isa,tana kokarin budewa taji yana Fadin”Meyasa kika ce zaki bini..?baki tsoron irin zaman da zai gudana tsakani na dake..? Waigowa tayi tana kallonshi sai taga baima juyowa ba, Fuskarsa tana kallon bangon dakin kamar ba shine bane,yayi mgana.
Bayanshi ta kurama ido,tana jin wani sanyi na Shiganta,Kasa mgana tayi illah kuramai ido kawai datayi,bata ankara ba taga ya juyo yana mikewa zaune bayan ya jingina bayanshi da gado,ido ya zubamata yana kallonta,kunya ne ya kamata sai kawai ta duka tana kokarin bude akwatinta taji yace”Ina tambayarki baki bani amsa ba,kuma kin tsaya kina kallona..,?”Ya Furta yana harde hannuwanshi akan kirjinsa..
Tana duke tace mai”Armmm me kace..? Wani kallo yayi mata kafin yace”Bansani ba kina nufin bakiji ni ba,bansan rainin wayau fa..?yafada muryansa acunkushe,diridiri tayi tana kallonshi Shiko ya sakarmata idanuwansa kamar zai daketa dasu,Sunkuyar dakai tayi tana Fadin”Kawai bani so kamin nisa ne..”Ware ido yayi yana Fadin”Really…? Saboda mene..?
Kanta na duke tace”Saboda bani son karatun dana fara ya tsaya ne..”Yamutsa Fuska yayi yana Latsa wayarsa datake ta neman Dauki,yana sakin wani kafirin mirmishi,yace”Ba gaskiya bane,ko bani ba akwai masu koya miki karatu,baga Ummi ba ga kuma hajiya ko Saleema,duk wanda kika ma mgana zai koyamiki..”Idanuwanta ne suka ciko da kwalla,sai kawai tajuyamai baya tana share hanci.
Mikewa yayi yana Fadin”Kinsan wani Abunda baki sani ba game dani? na tsani muna mgana da mutum ya juyamin baya,ko kuma yayimin tsaki? i hate does wlh..”Yafada yana daga kiran dake shigowa wayarsa bayan ya Fice daga dakin.
Ajiyar zuciya ta sauke tana bin bayanshi da kallo,agurguje ta saka rigar barcinta,doguwar rigace mai kalan ja da fari,hijabinta ta saka ta haye gado,ta lafe gefen datake kwanciya,Tun tana sa ran dawowarshu har wani barci mai dadi ya kwasheta bata farka ba,sai da taji yana tashinta da asuba,lokacin ma harma yayi alwala Sanye da jallabiya,yace tatashi tayi sallah ta shirya yana dawowa masallaci zasu Wuce.
Wanka tayi kafin ta dauro alwala,sai da tayi sallah kafin ta shirya cikin wani riga da Sikat,Rigar Farace da digon baki,sai sikat din na roba ne baki,yana da budewa daga kasa,sai vail dinta baki wanda ta yane kanta dashi bayan ta daure gashinta da band,Tana cikin sanya takalminta ne ya Shigo dakin,tana ganinshi ta rankafa tana fadin”Gud mrnig mallam..”
Mrning..”Kawai yace yana kallonta kasa,,kasa,kafin yace mata”Baki da wani kayane sai wadannan..”tana durkushen tace”Eh..”karamin tsaki yaja yana Fadin”Ok,.Kada ki dauki kayan duka juz akwatu daya ya isa,munje chan zansa adinka miki kayan mata mai mutumci..”Gyada kai tayi kafin tace”Tanque..”Bai amsa mata ya shige tiolet,ita kuma ta mike tana hada kayanta akaramin akwatunta guda daya.
Baijima ba ya Fito daure da babban Towel,kirjinsa na Fitar da maikon Ruwa kallo daya tayimai taji gabanta ya fadi,saurin dukar dakai tayi tana jin wani sanyi sanyi na Shiganta,bata jira komai ta Fice daga dakin kamar zata kifa saboda yadda jikinta ke rawa,da irin kallon da Saleem yake binta dashi,batasan dalili ba,ammh da zarar ya samata ido,shikenan sai taji tana neman rasa natsuwarta.
Tana Fitowa Falo babu kowa,kichen ta Shiga,nan babu kowa Ummi bata riga ta Fito ba,kila yau bata da zuwa aiki da wuri ne,dakin hajiya ta wuce suka gaisa,ta sanar da ita zasu tafi,tamata Fatan Allah ya tsare hanya,Sai da ta Fiti daga dakin Hajiya kana taga Ummi ta Fito,tana kokarin hada breafsat,gaisawa sukayi cikin girmawa,Fere dankali Ummi keyi Malika ta kariso zata karba,Ummi taki bata tace tabari kawai kada ta bata kyanta,suna cikin hakane sai ga Saleem ya leko yana Gaishe da Ummi,gabadayansu suka waigo,yana sanye da Suit Red and black,ya daure wuyanshi da bakin Tie,jakar brief case dinsa ne sagale akafadanshi yana duba agogon Fatan dake hannunshi ne yake cema Ummi..
“Ummi zamu wuce,ina da Meeting 12..”Wukar Fera dankalin ta ijiye tana Fadin”Da wuri haka saleem…? Fita yayi daga kichen din yana Fadin”,Eh Ummi,bari nayi ma Abbi sallama,Ke dauko kayanki ki Fito mana..”Yafada yana haurawa sama,Ummi tace”Maza kije ki dauko kayanki,Saleem bayason jira..”Jikinta asanyaye Ta koma dakin ta jawo karamar akwatunta tana kallon dakin cikin kewa,littafanta ta manta da hanzari,ta Daukosu ta saka cikin aljihun akwatun ta Fito,koda ta Fito Abbi da saleem sun Sauko kasa, har kasa ta duka ta gaishe da Abbi ya amsa yana tambayanta jikinta,ita kuma Ummi kichen takoma da hanzari ta Daukoma Malika Dambun nama dayawa cikin wata katuwar roba,ta damkamata karba tayi tana ta godiya,A gurguje Saleem ya Shiga bangaren hajiya suka yi sallama har bakin mota suka rakasu suna saka musu albarka,sai da motarsu ta fita daga gidan kana suka koma cikin gida cike da kewa.
*
Wurgi tayi da wayar bisa gado,tana zuba tagumi hannu bibbiyu,Nadira dake gefe tana kwance Ruf da ciki tana Danne danne bisa system dinta ta dago tana kallon Zahra take Fadin”Wht happend best..? Hawaye ne suka cikamata ido,ta girgiza kai tana Fadin”Best baya picking call dina,Tun Shekaranjiya nake kiranshi yana yankemin kira..”Tafada hawayen na zubomata.
Ture laptop din tayi ta mike zaune tana Fadin”Shine ya isa ya sakaki kuka..?Kara Narke baki tayi tana Fadin”Haba best,do u know how much i luv him? wlh inajin in ban aureshi ba zan iya mutuwa..?Tafada wasu hawayen nakara zubowa mata.
Cike da mamakinta ta karisa gareta tana Rike hannuwanta take Fadin”Kinga srry inaga baya kusa ne,kimai uzuri kibar kiransa har zuwa gobe,in bai kira ba,ni zan nemasa ta wayata,kinji..? Kan jikinta ta kwanto tana Digan hawaye tace”Sai dai gobe ki kirasa,saboda bazan iya jurewa ba har nan da wasu Awanni ba..’Kanta ta Shafa tana Fadin”Ok don’t wrry i will try my best,kibar kukan hakanan,yans tabamin rai kinsani..”Tafada tana dagota ta share mata kwallah tana Fadin”Oya smile..”
Nakwa nakwa tayi da Fuska alamar zata kara saka kuka,Saurin taro habanta tayi tana Fadin”Oya Smile aha..,Smile MRS SALEEM KABIR KUMO”Kamar ana tallar closeup,haka ta washe baki tana Rumgumeta take Fadin”Tanque my best..”
MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
