Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    “”Bai waiwayi Malika ba sai da tayi Shekara hudu aduniya,ammh duk bayan watan Duniya yana Turamata over 5k abankin madam dora domin hidimarta,shiko bashi wannan kasar bashi wannan duk domin yaga mafarkinsa ya tabbata,itako Malika tatashi hannun Kafurai ne,bata taba zaton tana da Sirkin kamshin musulunci ba.

    Madam Dora ita ta sanyata amkaranta,kuma mkrantan ma,na Turawa,shiyasa tun malika na yar karama dabi’unta da kuma hallayanta yakoma na Turawa,domin a iya wannan Shekarun batataba sallah ba,domin madam dora bata koyamata ba toh masulmace ita,balle ta koyar da ita,wanda yakamata yazauna ya koyar da ita neman Duniya ya Rufemai ido,banda zuwa coci da karatun,bibble bata koyamata komai,domin tayi alqawarin bazata bar Diyar Juliyat ta subuce mata ba, ko kafin mahaifinta ya karbeta ta riga da ta gama tusamata duk wani akidansu.

    Shiko Abdulmalik duk wani soyayyah da tanadi wa malika yake yinshi domin yana matsanancin sonta da kuma tsausayinta na yarda bata taba shan Nonon uwa ba,sai dai madara,kuma bata rayu da mahaifiyarta ba,Shiyasa ya dauki son Duniya ya doramata yakan samu lokaci yazo,domin yanzu yabar england yana kasar spain yana aiki da wani kamfanin sarrafa agogon Fata na maza da mata,gida kuwa sai dai yayi musu sakon kudi ko ya kirasu ta waya bai samun sararin zuwa.

    Sai da aka kirasa aka sanar dashi Innaro ta rasu kana yaje Nageria lokacin kuma Malika tagama primary sch ,t yaso ya taho da ita,ammh madam Dora taki yarda ta dinga kawomai uzurin cewa Ga mkrantar ta,kar yatafi da ita karatun ta yatsaya,ita kuma bata so yatafi da ita ne yan”uwanshi su Farga Da Abunda ke Faruwa su riketa yaki dawo da ita,ta haka ta ribaceshi ya tafi ya barta,sai dai yaje ya sanar dasu da baki,babu wanda yanuna wani damuwa domin lokacin Abdulmalik shine Sarkin gidan sakamakon yana da kudi yanzu so babu mai ce mai baiyi Daidai ba.

    Bai dawo ba sai Da ya bada kudadade sosai wanda zai bude wani kamfanin sarrafa atamfofi akano,domin yanzu Abdulmalik yana da hannayen Jari da yawa akamfanoni da dama,shiyasa yake da kyakyawan alaka da Turawa sakamakon yasan harkan kasuwancin da yadda zai habaka kamfani ya shahara lokaci kadan ba”a Rufe Shekara ba *DAN KASUWA INVESTEMENT* ajahar kano, ya kammallah kuma kafin lokaci kadan ya shahara ako”ina aka sanshi kafin arufe shekara biyu Alhaji Abdulmalik ya mallaki manya kamfanoni masu yawa agida Nageria,kama daga na sarrafa takalma,dana Sarrfa kayan yara maza dana mata,harda na taliya,sai kuma na Tumatur,bayan gidajen man dayake dasu wanda ya bude su da sunan *MALIKA MALIK PETROLEUM NIG LIMITED* Ako wata wata jaha afalin Nageria in kaje zaka ga brach dinsu,hatta a malumfashi bai san iyakarsa ba.

    Bai tashi karban Malika ba sai da tagama Secondry sch dinta a england lokacin tana da shekara 18 Aduniya duk inda girma da budurci yake to Malika tagama mallakanshi,ammh kallon Farko zakayimata ka shaida da mahaifiyarta take kama,don tafi kama da baturiya Fiye da jinsu hausa Fulani,duk da baban inda yazo yana kokarin nusar da malika cewa itafa ba irin dangin mamanta bane ita musulmace,toh zata jishi ne kawai ko ya takuramata tayi sallah na ganin idonshi ne kawai yana tafiya zata watsar takama harkan gabanta,tun tana karama ta iya zuwa party da club clubs gashi ta koyo banzan dabi”,an yayan Turawa na Shigar banza bata kunyar Fitar da tsiraicinta waje,gashi ,ammh wannan kwakwalwar ta mahaifinta tayi gadonshi wajen kokari da himma,Abunda yasa malika tadawo hannunshi saboda mutuwar madam Dora ce,yasa bayan anyi Shagalin binneta ya karbo malika tadawo hannunta wanda bai wani samu matsala da sauran yan”uwan mahaifiyarta ba,Tunda ya cikasu da kudi kuma yayi musu alqawarin kawota duk bayan wani Tsawon lokaci.

    A Canada Malika tahada digirinta na Farko akan Accounting daganan ta Wuce kasar America a babban birninta US tahada digirinta na biyu,bata dawo ba sai ta Hada takardan Phd dinta,lokacin shekaru biyu da suka Wuce mahaifinta yagama cin moriyar Turawa suma sunci nashi yasa ya tararra yakoma gida akatsina ya gina wani tamfatsetsen gida mai kama da aljannar Duniya,kuma yayi aure da matarsa Hajiya Binta,yar”uwansa ce suka manna masa,saboda kudinsa,duk da ita Binta bata sonshi,dayake bazawarace,mijinta ya rasu ya barta da Diya daya mace JODA wacce bazata wuce Shekara 22 da biyu ba, ammh dole ta hakura Tunda kowa na Son daula ,uwa uba kuma tasamu jin dadin Rayuwa,domin shi ya kaita makka,kuma suna zuwa yawon duniya duk bayan wata daya bayan ya saka Joda a mkranta ,yanzu haka tana Final year dinta ne Barrau dikko dake zaria tana karantar SB NURSING.

    Tun zuwanta gidan Ta fahimci daga yar har uban babu mai tarbiya da ilimi gabadaya jahilci na dawainiya dasu ranar da suka fara kaima Malika ziyara a US sai da ta zubar da kwallah yadda ta ganta da irin Shigarta da yadda ta maida rayuwarta wlh ko wasu Turawan Sun fita kyan gani,gashi ya shagwabata ya sangarta baya iya mata Fada,yanzu sai takama kuka tana hargowa,shikuma baya son bacin ranta Shiyasa duk Abunda tagama dama shi takeyi,gashi Tun tana karama kudi sun batata komai take bukata aikwai Shi bata taba neman wani abu tarasa,tun dataji lbrin mahaifinta yayi aure,taji tsani matar tukan ta ganta,sai gashi sun hadu banda harara babu Abunda ya shiga tsakaninsu,sai ma ita Hajiya binta ne Alhaji Abdulmalik ya umarta data gaishe da ita Malikan saboda lalacewa,koda suka dawo gida,ta nemi gayamai gaskiya game da yadda yabari Rayuwar malika ta lalace tana ya”mace,ammh sai yaki bata dama yace ta kyaleta taji dadin Rayuwarta Allah yaba mahaifinta Dukiya mai yawa so Dole tayi Abunda taga dama.,Tundaga Ranar Hajiya binta takawo ido ta sanya musu bata kara saka Musu baki ba, Ba kome zasuyi tasani akwai ranar kin Dillanci.

    Bayan tagama karatunta dakyar Alhaji malik yashawo kan malika tadawo Nageria da zama saboda kula da kamfoninsa,saboda malika yarinyace mai kokari,she is very talent and smart,gata da wayau da kuma lura,shiyasa lokaci kadan Alhaji malik yasakarmata duka ragaman Kamfoninsa,domin ya Fahimci tafishi iya gudanar da komai,shi sai dai yana gida suyi waya agudanar da komai ita kuma malika taje ta tabbatar,kowani taro za’,ayi,daga gida Nageria zuwa kasashen waje duk malika ke Zuwa ta gabatar da kowani ragama,shiyasa kafin lokaci kadan Tayi suna Aduniya don Aduniya inda kafarta bai taka ba kadan ne,kuma babu wanda baisan Rashin tarbiya da rashin mutumci irin na Diyar Abdulmalik Dankasuwa ba,abokansa sunsha zuwa suna kokarin mai nasiha ammh duk sai ya toshe kunni,daga kuma ranar ya yanke alaka da mutum,masu kwadayi kuwa sunsha kawo tallah da tushen hada ya’yansu aure da Malika ammh yaki bin mganarsu domin malika yanzu ba aure bane agabanta batama sanshi ba,domim bayan dawowarta dakyar da yaki yarabata da karatun Bibble,dakyar kuma ya ke sata tana sallah ammh wani lokacin,sai tazo kwanciya take hadawa,tana Tura bakin ita an takurata tafison Rayuwar england taje coci taje Club,tayi yawo yarda taga dama,ammh dawowarta Nageria,yasa duk tazama atakure ga wani takuran wai sai ta dinga sallah,ita wlh bazata iya ba,mganar dressing dinta kuwa Shi baya ganin aibun hakan,domin rashin saka dankwalinta yasamo nasabane da tashin datayi cikin Turawa shibaya ganin hakan awani mtsala Tunda shima ba ilimin addin yake dashi ba.

    Shiya samomata masu kula da ita mata har guda biyu mrry da Dose,sai excort dinta harsu ashirin masu take mata baya,in zata Fita kamar wata yar Shugaban kasa yadda combain yake biye da ita,ko kafin kace kwabo Alhaji Abdulmalik Dankasuwa yashahara kuma yayi Fice Aduniya bayan tarin dukiyan dayake dashi,ga kuma manyan hannayen jarin daya ke dashi akamfanonin kasashen ketare,inda malika take kula da Shige da Fitar komai,saboda hakanema yasa tayi karatu akan ilimin na”ura domin ta saukakama kanta wasu al”amuran rayuwa ta yau da kullun Tunda komai na business din mahaifinta ita ke kula dashi.

    Sau daya tataba zuwa malumfashi,ammh sai da tayi danasani saboda gabadaya garin bai mata ba,kama daga yadda aka dinga kallonta kamar anga wata bakuwar hallita,saboda yanayin shigarta uwa uba babu kallabi akanta sai gashinta data daureshi ta baya ta bazoshi,ba mutanen garin ba hatta dangin Abdulmalik ranar sunyi tir da Dabi’un Malika da suka mata mgana tayi musu Rashin mutumci ta zagesu tas tayi tahowarta,da suka kira mahaifinta suka sanar dashi sai ya goyi bayan yarsa yakuma ce ko suzo subata hakuri ko kuma ya cire hannunshi akansu,sanin da sukayi in ya cire hannunshi akansu sun bani sun lalace don basu da kamarsa yasa sukayi mota guda suka zo suka ba ma Malika hakuri wanda sai da baban yasa baki kana tace ta hakura,Tunda ga lokacin kowa yake kiyayewa saboda ita bata ganin kowa da daraja sai mahaifinta bandashi kowa zata iya takashi saboda kudi,tana ganin Duk wani mikamin Duniyan nan bashi da wani amfani in ba kudi ba.

    Malika ta zarce Duk Tunanin mai karatu ba yarinya bace shekaranta 27 Aduniya ammh in ka ganta sai kace yar Shakara 20 ce saboda yadda ta mori jiki,babu gidan Talabijin da gidan Jaridun da ba”ayi hira da ita ba,shiyasa sunanta yafi na mahaifinta shahara aduniya,malika ko abinci bataci da kanta bata akeyi ko wanka sai anyi mata saboda gata komai da kuka sani yimata ake,saboda tace matukar kudi na mganin komai to zasu mata mganin dukkan mtsalanta,Dawowarta Nageria basa ta rage zuwa clubs da party wani lokacin sai tsakiyar dare take dawowa Akullum Alhaji Abdulmaleek Dankasuwa yana takaichin hallayar Malika musaaman ma n zuwa club da party,ammh bashi da yarda zaiyi da ita,don baya iya tsawarta mata ba, kana tana da wayau bata da yarda ko kadan,ko ma”aikatan ta da excort din ta bata yarda dasu ba,tana ankare dasu kuma tana bibiyan dukkan motsinsu.

    Abu dayane batayi Shine Zina,Malika bata yarda Akala tashiga tsakaninta dawani Namiji ba,sai dai in ta kasuwanci ko kuma abota,shima tun barowanta US rabonta da abota da Namiji,kuma tun alokacin ne da Sunan Abota take yarda tayi kiss da mutum sai dan Abunda ba”a rasa ba,ammh bata yarda wani yaketa mata budurci ba,saboda tana da bala”in wayon tsiya shiko mahaifinta tunda ya samu ya yakiceta da zuwa coci da karanta bible hankalinshi ya kwanta,sauran abubuwan datake kuma ko Abun na damunshi bai iya mata mgana Saboda yadda yake matukar sonta da kaunarta,so daya yataba kwantatan yimata Fadan ta rika sanya kayan hausawa,kuma ta dinga mutumta Hajiya binta, da malika tayi Fushi sai dai kawai yasamu waya kan cewa tana England takoma wajen dangin mamanta hankalinshi yatashi sai da yaje da kanshi dakyar da lallashi ta yarda zata dawo ammh da sharadin bazai kara takuramata ba,dole ya yarda da haka saboda yana Tsoron kada watarana Malika tayi Ridda takoma Kafura,duk ko ayanzu marabanta da kafurci ne kadan ne,banda sallah bata wani Abu na bautar Ubangijinta.

    itama sallar ba da kyau takeyi ba,ko Fatiha banajin tagama iyawa Saboda lalace babu Abunda tasaka agaba sai Duniya tanaYin duk Abunda tagama dama,ko dabi”ar Tubewa zindir wasu matan nayi miki wanka,Ai dabi”ar yayan Turawa ne wadanda basu san addini ba,ammah kome malika ta zama Aduniya sanadin yana wuyan mahaifinta domin Tun farkom gina Ginshikin samunta bai bi yarda Addinin mu ya tsara ba,koda aka umarceka ka auri Ahlul baiti bai chanchanci bayan haihuwar malika ya mikama Turawa rikon yarsa ba kuma yana sane da cewa sudin ba musulmai bane,taya zasu so malika ta koyi addininshi,shiyasa suka koyar da ita duk dabi”unsu da addininsu saboda ko gaba kada ta barsu.

    Ranar da suka hadu da Saleem har ta mareshi ta dawo Daga kaduna ne,wani party ne na ya”yan manya marasa jin mgana da”aka Shirya to daya daga cikinsu Friend dinta ne,Tun suna US shiya gayyaceta taje,shine da zasu dawo sukayi dare har su Saleem suka taremata motoci,Tun sadda Abun yafaru batakara Tuna wani hallita ba balle ta damu da Furucinsa na sai ya rama, ita tana ganin Shirmene da yarinta da kuma talauci da rashin nayi ke damunshi yasa,tun awajen ta tararrashi ta watsar ta cigaba da harkan gabanta,duk a iya tsawon wannan Shekarun babu Abunda ya ragu na Hallayar malika saima Abunda ya karu,Hajiya binta ko bacin kashin da bata gani har marinta malika tatabayi,ammh Alhaji malik bai dauki mataki ba,ita da banza Duk dayane,kallonsu kawai take tana jiyema Alhaji Ranar da zaiyi nadamar Turban daya dora Tilon yarsa akanshi.

    Tsakanin Malika da Joda ko basu da wani kyawawan alaqa,duk da ba sosai sukayi haduwa ba,wani lokacin in Malika na gida Malumfashi Joda ke Tafiya saboda ita yarinya ce mai hankali da gudun zuciya ga natsuwa,gata bata hayaniya,itakadai sai ta Shige daki tana kuka,in taga cin kashin da malika kema mahaifiyarta.

    Abun na damunta ammh bata da yarda zatayi sai hakuri saboda ko ita bata da bakin mgana, Saboda akwai lokacin da Makila tama Amminta rashin kunya,sao tayima malikan mgana,shikenan ta juyowa ta kasheta da mari,ta kuma sanya su Peter suka Dauketa chak suka Fita da ita daga gidan,tace kuma zamanta yakare agidan,sai dai Hajiya binta ta bita wajen tabata kudin mota tace ta tafi malumfashi Abun yamata bakinciki,sosai datatafi malumfashi tadade wajen Dangin babanta kafin ta dawo,shima saboda Ammin nata ne,ammh daga Alhaji Abdulmalik din har Malika ba wanda ya nemeta,sai ma goyon bayanta da yayi lokacin da hajiya binta ke sanar dashi Abunda tayima jodan,tabe baki yayi yace tayi Daidai Domin tana da iko da gidan Ubanta,Shiyasa Tundaga lokacin ta kiyayi kanta da malika.

    Iyakarta da malika sannu daga haka wata mgana batataba Shiga tsakaninsu ba,sai suyi kwanaki agidan ammh wlh ko zasu hadu sau goma ne ba wacce zatama wata mgana,ita malika tana ganin tafi karfin joda,saboda gidan mahaifinta take zaune,kuma take ci tasha tayi Sutura daga Dukiyar ubanta,to tana ganin tafi karfinta tsakaninta da ita kamar nisan kasa da sama, ne.

    Itako Joda tana kiyayewa ne Tun Abunda yafaru Amminta tajamata kunni sosai kan Malika,shiyasa tafita harkarta in taga damane ta gaisheta randa bata ra”ayi kuma tayi kamar bata ganta ba.

    *CIGABAN LABARI*

    _Washegari_

    Saleem Tun bayan da suka dawo sallar Asuba da Abbi da ya marwan bai yarda ya kara haduwa dakowa ba,ko masallacin ana sallame sallah yayi Wuf ya Fito,saboda kada ya marwan ya tareshi da wata mgana,don bai shirya amsama kowa tambayanshi ahalin yanzu ba,sai ya aiwatar da gudirinsa akan Malika

    Yana dawowa ya Shirya domin komawa bakin aiki,ada yaso yabari sai gobe monday,ammh don gujema Fuskartar wasu barazanq mussaman ga Ya marwa da Ummi,shiyasa ya Shirya komawa batare da ya sanar da kowa ba.

    Karfe 7:00am na Safe ya Fito daga Dakinsa yana sanye da Uniform dinsa,sai wayarsa da makullin motarsa,Falon Tsit babu motsin kowa sai Ashura mai goge goge ce kadai afalon tana share share,sama sama ya amsa gaisuwanta ya nufi koridon da zai sadashi da dakin Hajiya babba,domin itace kadai hope dinshi ayanzu.

    Koda ya Shiga dakin nata,tana zaune akan darduma tana laziminta na safe,domin a akidar hajiya in tayi sallar asuba bata tashi awajen sai Rana ta Fito.

    Tana jin sallamarsa ta dago tana kallonsa,saboda yadda uniform din suka amsheshi ko ita sai da yayi ma kwarjini sosai,mirmishi ya sakarmata kafin ya karisa gabanta ya zauna bayan ya cire takalmansa daga bakin kofar dakin,yana Fadin”Hajiya barkanmu da Safiya..?

    Shafa addu”anta tayi kafin tace”Muntashi lafiya? sai ina naganga cikin Shiri kamar wanda akace gawani dan fashi chan? Dan mirmishi yayi kafin yace”Kaji hajiya,yo mu ai basai mun jira ance ga Dan fashi ba,mu da kanmu muke Fita nemansu,Tunda kinsan bazasu kawo kansu ba..”

    gyada kai tayi tana Fadin”Hakane kuma toh Allah yayi jagora..”Da Amin ya amsa kafin yace”Hajiya zan Wuce,nazo ne nayi miki tuni kan mganarmu ta jiya,wlh am serious don Allah ki matsama Abbi yaje yanemanin Aurenta plz..”Kai tsaye hajiya tace”Ina zanyi sanya,ai dolensa nema yaje,Abunda muke ta nema kuma Allah yakawo to me zamu jira?karka damu insha Allahu zaka aureta Tunda na lura kana sonta..”

    Dan cije baki yayi baiyi mgana ba,saima Kallon agogon fatan dake hannunsa yake,kafin ya mike yana Fadin”Zan Tafi hajiyata,nidai kiman kokari kome ke nan,zamu waya..”bata tashi ba tace”Toh Allah ya tsare…”Da Amin ya amsa kafin ya Fice.

    Daga Dakin Hajiya ko Dakinsa bai koma ba,yayi waje,motarsa ya Fada yamata key yana zuba hon,da hanzari maigadi yazo ya budemai get yana mai Fatan isa lafiya,babu wanda yasan Tafiyarshi agidan sai hajiya,shiyasa har sai da akazo breafast ne,aka Farga saleem bashi agidan lokacin da Marwan ke tsiyan yasan Abunda yayi yaki Fitowa Hajiya ce tace”,Wa..? Salihu ai ya dade da isa zamfara yanzu…”ba su kadai ba hatta da Ummi sai da Abun na Saleem yafara bata mamaki babu dai wanda yace kanzil kowa ya barsa da Abun Tunda ganin Shikanshi mai gidan bai ba mganar wani muhimmanci ba.

    shiko Abbi yaki bada Fuska ne saboda kada sumai wata mgana mussaman Ummi wacce Tun daren jiya taso tatadamai Tsiyarta yaki bata Fuskar yin hakan,data fara zencen ita bata yarda ba,kuma shima kada yabiyema Saleem,haryanzu yaro ne baisan inda ke mai ciwo ba,ammh ita bazata bari Akawo mata wannan Tsinanniyar yarinyar amtsayin Suruka ba ko alama.

    Shikanshi Abbi ya Shiga dogon Tunani game da bukatar Saleem,duk shima yana da lbrin yarinyar kaf bamai dadi bane,toh ammh yayi Duba zuwa ga wani Abu,duk wanda yayi sanadiyar Shirriyan wani Shima yana da lada,sai dai kuma kafin ya je wajen Mahaifinta sai ya kira Saleem ya tabbatarmai ba saboda Dukiyan mahaifinta yakoson aurenta ba,duk yana da Shaida sosai kan tarbiyan ya”yansa,.

    Baya da Haufi kan Saleem domin yafi Shakuwa dashi fiye da marwan,wanda baima yi karatunsa a nageria ba,kuma yana da masaniyar Jarumi ne na karshe,wanda zai iya tankwasa ko wacce mace indai tana karkarshinsa ne,kuma aure ba haramun bane,sunnar ma”aiki ne kuma Dukkansu akanshi sukazo Duniya,shiyasa batare da shawara dakowa ba ya yanke zai kai ma Alhaji malik ziyaran Farko tun bayan kammallah jami”ar Dan Fodiyo basu kara samu zama sosai ba,sai dai haduwa sama sama,wanda bayan yazama IGP sun hadu sau biyu wajen taro wanda shima agayyaceshi ne yaje suka hadu,suka gaisa duk da kowa yana da nombar kowa,ammh basa mgana awaya,saboda yanayin aiyukan kowannensu.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!