Search
You have no alerts.

    Samarin Bana Chapter 1

    [10:45PM, 02/11/2016] Rahamat Nalele: 👯👯👯👯👯

    *SAMAREEN*

            👯  *BANAH*

           👯👯👯👯

    *TASU SALAN SOYAYYAR*

    *Na Rahamat Muh’md Rufa’i Nalele*

    Part 1…..

    *Nutsu da kyau me karatu ka karan farkwan labarin nan da kyau kuma kar kayi gigin mantawa. Dan xai temakema wajan gane ya abin xai kasance nan gabah*

    Sunana  SAILUBAH KASIM.

    Ina garin KANO da xama awata unguwa da akekira fage

    Ina da shekara ashirin da biyar aduniya wato 25 years

     Na kasance mace mace kyakkyawa san kowa in wanda ya rasa

    Ni farace soll doguwa me kyan bafali

    Ina da hq da breast na ‘daukar hankali

    Bancika qibaba sannan baxa’a kirani siririya ba

    Komai nawa ya ha’du kamar yanda kowace mace takeso ta kasance

    Idan na kalli kaina a mirror hmmmmmmm

    Dole najah numfashi anan

    Dan ni dake da kai bana buqatar kufitoh kuce

           Ya SAILUBAH kin ha’du

    Na sauke alqur anin me girma inada ilimin  addini daidai gwargwado dan baxa’a kirani jahila ba

    Ayanxu ina U:J ina fannin san kasancewa cikakkiyar doctoh

    Sai dai bawani damuwa nayi da karatun bah dan inada burukan da suka shige min gaban karatun

    Na kasance mace mesan ku’di

    Mesan na mallaki gida da mota

    Sannan ku’di su ratsani

    Inasan namiji ‘dan gaye ‘dan kwalisa me ilimi wayayye me hankali

    Sannan ya kasance miskili ya kasance ni ka’daice xan mallaki dariyarsa da komai na halittarsa

    Ya kasance nika’daice tasa abin dubawarsa  amma in aka cire iyayansa da qannansa

    Ya kasan me hakuri sannan me kishi akaina 

    Ya kasance naxama nice madubin dubawarsa. Shikuma yaxama shakallo agareni

    Ina da burin Auran Attajirin Alhaji me ku’di da nera

    Irin Alhazawan garin abuja nan

    Maso ku’di da albaxaranci

    Bana burin Auran qaramin yaro kamar wanda ya girmeni da irin shekara uku haka

    Na fisan na Auri wanda yabani akalla shekara goma sha biyu

    haka na saka araina baxan ta6ata auran qaramin yaro bah. dan na raina qarfinsa da jarumtarsa

    Acikin unguwarsu akwai wani gida me kyau da ‘daukar hankali wanda ya kasance gidan xuwana ne ako da yaushe naga damar xuwa

    Inada aboki RAMADAN wanda shine ya kasance wanda yakejin sirrina

    nayi matuqar shaquwa da RAMADAN irin shaquwar nan da akekira da inbakai baxan iya rayuwa bah

    Ina san RAMADAN dan ya kasance yaro memin ladabi da biyayya duk da shi ‘din miskiline

    Amma ya ha’du tako ta ina dan  ina qaruwa dashi tako ta ina

    Dan yafini ilimi yafini hankali sannan ya fini nutsuwa

    Duk shawarar da nanema agun  RAMADAN idan yace min iyi kasa bar kaza nabarshi har abada

    Yaro ne qarami ‘dan shekara ashirin  cif ba qari ba rage ayau

    Idan me karatu ya koma baya toko xai gane naba RAMADAN shekara biyar kenan

    Saidai RAMADAN funannan yaro ne. Xaki gane waye shi idan tafiya tai tafiya

    Tunda natashi banta6a ganin idan mahaifiyata bah 

    Dan tada’de da rasuwa tun ina jaririya

    Ayanxu dai ina hannun matar babana ko ince muku Kakata

    Ba lefi suna kula dani sosai saidai matar babana tana da san ku’di ba nawasa bah

    Amma duk da san ku’din nata nafita

    Babana dacan yayi ku’di Sosai daga daga baya ne karayar arxiqi tasa meshi

    Ayanxu bashi dashi Saidai bama rasa na sawa abakin salati

    Abu ‘dayane ya bari adukiyarsa. shine gidanmu.

    Gidanmu babban gidane kuma ginin xamani

    Dan a unguwarmu in kacire gidansu Ramadan akyau toh cika saka gidanmu

    Inada qawaye masu bu’dad’dun ido da wayewa fiye da tunanin me karatu

    Wannan shine labarina akataqaice

    👯👯👯

    Sunana RAMADAN Nasir yaro ‘dan 20 years

    Na kasance ina da buri ‘daya arayuwata shine

     natashi da maseefar san wata mace me kyan sura. Da komai

    Tayi tako ta ina

    Ina santa

    Ina santa

    Ina santa

    Ina da abokana ye biyu Fawas da Khamis

    Duk ra’ayinmu ‘daya yake dasu

    Amma mutane da dama suna cewa nafisu nutsuwa da hankali

    Na kasance ‘dan gaye me san tsafta da qamshi

    Duk unguwarmu ni ka’daine nafita xakka a iya wanka

    Dan nayi xaman jos anan nasamo Sirrin

    Inada kalamai masu tsayawa  arai

    Sannan Auntyna Tace ni futunanne ne

    Ya ta6e baki sannan yaci gaba da cewa

    Idan hakane Ku da kanku xaku sheda hakan idan kuka cigaba dabin Aunty Rahamat Nalele

    Suna na KHAMIS

    Inada shekara ashirin daidai yau

    Ban tsaida wani buri araina ba tukunna

    Sai dai inada san mata saboda Suna sani nisha’di. mata abin farin cikine kowane ‘Da namiji ne

    👯👯👯👯

    Suna na FAWAS

    Inada shekara ashirin daidai yau

    Ina da San mata Sosai kuma inada burin Auran mace wacce ta xarce shekaruna da kamar shekara biyar haka ko shidda

    Kuma bana san Auran wacce ta Waye nafisan Auran ‘Yar qauye me halin yarinta

    Tab😳

    👯👯👯👯👯

    Suna na Zainab Amma ana kirana da XEE dan nafisan akirani da hakan

    Inada shekara ishirin da biyar.

    Ina da saurayi Surajo ina matuqar sanshi da kishinsa

      Sannan ni ta hannun damar SAILUBAH CE dan duk acikin qawayanta nice babbar qawarta

    👯👯👯👯

    Suna na Hameeda Ya’u ina xaune a qauyan takai Babana ya rasu Mamana mah haka

    Ina hannun qanwar babana Innah Hansai

    Ba qaramin ganamin axaba take bah

    Duk aikin gidan ni nakeyi duk wani aika ni nake xuwa mata haka duk wani Girki ni nake yi

    Duk da ko tanada yara Amma Sam bata sakasu sai ni

    Sosai nake hango tsanata acikin idanta

    Bata sona bata qaunata

    Ta hana duk wani saurayi tsayawa dani wai tafiso na xauna inta yimata bauta

    Ayanxu shekatata ishirin da hu’du 24

    Bani da wani buri araina sai na kallan cigaba da bautar da nakeyi

    *Toh Madallah masu karatu kunji tushen kowa acikin wannan littafi nawa. dan haka sai kugyara xama kusha karatu*

    SAILUBAH yarince maisan ku’di kamar yanda tafa’da

    Amma duk ku’din da xata samu basa rufe mata ido

    Dan ko yanxu SAILUBAH tasamu ku’di xata iya kyautarsu gabaki ‘daya dan Allah yayota da San temakwan mutane

    Tana da kyauta Sosai ba ‘dan ka’dan ba da tausayi

    SAILUBAH ‘Yar gayece Sosai

    Duk unguwarsu ba’ayi yarinya me wankanta bah

    Zama na musamman samarin layin nasu suke dan kawai suga fitowarta

    Duk unguwar ba  wanda baisan SAILUBAH da halinta ba

    Kyauta San Mutane San ku’di fa’dar Gaskiya…………..

    Koda ko kar sa’an babanta ne kayi abunda bai dace ba  toko ba shakka saita wanke ka da soso da sabulu

    Duk unguwar ba Wanda baisan sha’kuwarta da RAMADAN ba

    Suna San junansu Sosai dan shi’din abokinta ne

    Mutane da dama idan sukaga SAILUBAH da RAMADAN xasu skull dake skull ‘dinsu ‘daya ba qaramin sha’awa suke basu ba

    Fa’di suke tsakanin SAILUBAH da RAMADAN wayafi kyau ne

    RAMADAN Yarone me hankali da nutsuwa

    Sam baya shiga sabgar daba tashi ba

    Komai xaiyi anutse yake yinsa

    Baya ‘daukar raini

    Yarone me farin jinin jama’a musamman mata

    RAMADAN na kowa ne dan Allah yayoshi da kwarjini

    Duk inda kika kai da abinki idan kikayi toxali da RAMADAN sai kinso Ki mallakeshi a matsayin mijin Auranki

    Ya ha’du ne tako ta ina RAMADAN yayi

    Yana da da’din murya haka kallo ‘daya xaki mai kisan anyi balaraban yaro

    RAMADAN cikakken ‘dan rainin wayone

    Sam baxa ki gane inda yasa gaba ba

    Yana ji da Auntynsa SAILUBAH. Sam baya San 6acin ranta

    Duk Wanda yake tare dashi yasan da xaman wannan

    Sai dai fah ahakan baqamin takurama SAILUBAN yake ba akan samarinta

    Shi ka’daine namiji agidansu

    Kuma Wanda kamanninsa yafita daban dana kowa

    Sam RAMADAN bai ibo Komai na iyayan nasa bah

    Mutane na mamakin wannan yanayi yanda RAMADAN ya futa xakka agidan nasu

    Kome yasa hakan

    (Tabbas kwakwalwa tana buqatar caji agun🤔)

    Su ukune agun mahaifan nasu

    Akwai yayar RAMADAN Saudat wacce ta kasance qawar SAILUBAH

    Sai shi RAMADAN ‘din

    Da qanwarsa Khairat

    Mahaifinsu Alhaji Naziru me ku’dine Sosai

    Ya shagwa6a Su da ku’di Sosai

    Haka ba qaramin SOO sukema RAMADAN ba

    Kome yasa haka🤔

    RAMADAN Yana da San karatu Sosai gashi da ilimi tunda ya taso ya fara xuwa makaranta bai ta6a fa’duwa akan Komai bah

    Yanxu haka saura bai fimai 1 year ya gama kammala karatunsa ba

    Inda yake san xama cikakken likita wato doctor

    Yaxama kenan ra’ayinsa ‘daya da Auntyn Sa SAILUBAH

    Idan Nace muku RAMADAN ‘dan rainin hankali ne karku musa min

    Haka KHAMIS iyayansa Suna da ku’di Sosai shima an shagwa6a shi Sosai da ku’di

    Su biyu iyayansa suka Haifa

    Ianada Yaya Rahamat tayi Aure tana garin Abujah da xama

    Ganin hakan KHAMIS shi ‘daya shiyasa shi abinda yakeso kuma iyayansa suka biye nasa

    KHAMIS Yanada San karatu inda yakeso yaxama cikakken loya Wato ya karanci low

    Shiko FAWAS iyayansa shi ka’dai suka Haifa

    Ba qaramin ji dashi suke bah

    Sun shagwa6a shi da ku’di Sosai

    *To Madallah me karatu gyara xama*

    Yau take talata kuma antashi da ruwan sama yaf yaf yaf gwanin sha’awa

    SAILUBAH sauri sauri gudu gudu takeyin Komai dan sunada karatu qarfe tara

    RAMADAN ya shigo falan hannunshi ‘dauke da Wasu takaddu Yace Auntyna lokaci ya fara tafiya fah

    Da sauri tajuyo xatayi magana sai kuma tatsaya kallansa kamar alokacin ta fara ganinsa

    Ya ‘daga mata gira tare da qarasowa kusa da ita ya kar6i ‘dan kunnan hanunta Yace in saka miki ko

    Tayi saurin ‘dagamai kai Tace kayi kyau Sosai Qanina

    Yayi Murmushi Yace Nagode Auntyna

    Gyarawa Sosai tayi  ya saka mata ‘dan kunnan ta’dauki gyalanta da ‘yar jakarta tamaqala

    Idan RAMADAN na kanta yana qare mata kallo. Ta ‘daga mai gira

    Yayi murmushi Auntyna tsaya na  photo

    Wayanka saita cika da pix ‘dina

    Yace in bake acikinta Wlhi bata da amfani

    Tace kayi breakfast kuwa

    Ya ‘dan Sosa qeya Yace nayi

    Tabishi da kallo ka’dan hmm bakayi ba

    Yace toh Kinga lokaci yayi……..

    Cire gyalanta tayi tashiga kitchen kawai. RAMADAN yaja numfashi tare da kallan agogo yana tsaki

    Bai ankareba sai gata qatan faranti ahannunta.  Wanda ke ‘dauke da lafiyayyan tia da kuma  soyayyan dankali da kwai

    Ta dire a gabansa Tace nabaka minti uku kayi Maza

    Yace Aunty banajin yunwa…

    Ta katse shi da jefa mishi wata muguwar harara

    Bashiri ya fara ci   

    Yayinda ita kuma ta xauna tana amsa waya

    Hello Alhajina ina kan hanyar xuwa makaranta

    Yace Amma naso inxo in ganki yanxu. Plx Ki bani ha’din kai yanxu naganki

    Aini takace. Kabari ina dawowa xaka ganni.

    Yace toh Allah  ya dawomin dake lafiya

    AmEEn Nagode. Tafa’di hakan da kashe wayan

    RAMADAN najinta Yace Auntyna dawa kikayi waya

    Ta gallamai harara cikin ‘daure fuska Tace ban sani bah

    Yayi Murmushi Yace pls gayamin Wlhi ba’abinda xai faru

    Tace hmm yama faru Wlhi saina baka mamaki idan kayi sanadin da Alhaji Jamilu ya dena xuwa gareni

    Ya kalleta ka’dan dayin murmushin rainin hankali Yace baxanyi Komai bah Auntyna Amma dan Allah gayamin yaushe kuka ha’du da har ya kasance ban sani bah

    Tace jiya muka ha’du a jifatu yaje siyayya

    Amma shine ko  jamishi aji bakiyi ba kika amsheshi daga ganin farko

    Ta gallamai harara Tace ban jah mishi ajinba

    Yace me yasa

    Cikin maseefa Tace saboda shi me ku’dine yayimin tun kallan farko dana masa

    Yace Amma………

    Tayi saurin katse shi da cewa. Wlhi RAMADAN ba wani abu daxaka fa’damin inji inbar mutumin nan dan yana da ku’di Sosai

    Kyautar farko daya min jiya dubu ‘dari uku ya ban 

    Yace haba Auntyna……

    Na rantse da Allah ka cikani da surutu xakasha mari

    Shuru RAMADAN yayi yaci gaba dacin abincinsa

    Can ya kammala Yace toh mutafi ko. Yafa’da da ‘daukar Wasu takaddunta

    Suka fitoh ya bu’de mata gaban motarshi tashiga shima ya shiga da jansu suka ficce daga gidan

    Direct gidansu XEE sukayi Suna parking tana fitowa

    Tayi kyau Sosai cikin shigar riga da siket ‘yan kanti

    Ta shiga motar ta xauna tana mita wai basuxo da wuri ba

    RAMADAN Yace lefin Auntyna ne fah

    Tace aina sani tasaka gaba kayi breakfast ko Yace ko shakka babu.

    SAILUBAH Tace hmm kema kisan inba ni’din nasashi gaba ba baci xaiyi ba

    Haka dai sukayi B;U:K university.

    Sunayin parking wata kyakkyawar budurwa tayi saurin isowa garesu

    Cikin rashin kulawa SAILUBAH da XEE suka fito dayin department ‘dinsu

    RAMADAN yafitoh da Murmushi akan fuskarshi Yace ha’a kaga kyakkyawar yarinya. Tauraruwa me dishashe hasken taurari. Gayamin me ya tsaidake a wannan lokacin da yadace ace kina can kina ‘daukar darasi

    Cikin jin da’di da dariya akan fuskar Amina Tace baxan iya fahimtar Komai ba inhar banganka ba

    Tunda naxo idanuna suke min ra’da’di dan rashin ganinka da basuyi ba

    Yace toh gani sun ganni sai hankalinsu ya kwanta

    Tayi Murmushi. Xanso muje shan iska anjima

    Ya kulle motar tashi yana fa’din xanfi kowa farin cikin hakan. Maxe jeki kar darisa Su wucceki da yawa

    Ba musu Amina tabar gun cikin jin da’din Ganin masoyinnata

    Gab da RAMADAN xai shiga department ‘din nasu

    wata ta tareshi da sauri

    Ya dafe kai cikin Murmushi Yace yane Asma’u

    Xuciyata bugawa take in bata ganka bah

    Amma na lura Sam xuciyarka bata damu dani ba Sam

    Haba nutsuwata abin kwanciyar hankalina. Wlhi dake natashi araina

    Meyasa toh kakasa nemana

    Kin sanni da karatu banasan nayi missing ‘din Komai. plx nutsuwata Ki lamince min nashiga na miki alqawarin yau xan baki lokaci na musamman dan kimallaki kalmomina

    Tace toh Allah yasa ina maka fatan alkairi

    Ya shigeta yana cewa tare dake……..

    Karatu ne Wanda sukayin shi cikin nutsuwata ahaka suka tashi inda SAILUBAH ta kalli RAMADAN Tace Amma fah abubuwa da dama na kasa fahimtarsu

    XEE tayi dariya Tace aike Kullun a haka kike

    Tayi Murmushi dacewa ai banda matsala tunda gani ga Qanina.

    RAMADAN Yace aikuwa ammafa Auntyna  kidinga lura saboda wata ranah.

    Taturo baki da cewa toh naji muje gida nafara jin yunwa ba sai mun jira KHAMIS ba …….

    KHAMIS ‘dinne ya katsesu da fa’din dawai tafiya xukuyi kubarni bayan yasan yau ban fitoh da mota ba.

    XEE ta kafeshi da ido Tace ya fa’da mana

    Ammma fah kayi kyau sosai  Tafa’da da shigewa motar Ganin SAILUBAH da RAMADAN sun shige.

    Yayi Murmushi Yace kai Aunty XEE ina wani kyau anan. Yafa’da shima yana mai shigewa cikin motar

    Cikin nutsuwa RAMADAN yake tuqin motar

    KHAMIS Yace Kasan wani abu

    Sai ka fa’da

    Wlhi fitowata ‘daxo na ha’du da wata xanka’daxiya……

    Ta ha’du Sosai dan tatara duk wani abinda kowane ‘da namiji yake buqata awajen mace

    Dana kai agoge min motata tsayawa nayi daniyar agama goge min natafi da ita

     lokacin ko wanka banyi ba

    Sai gata tayi parking motar tata akusa dani

    Ta fitoh tana wani yauqi da rangwa’da. dan Allah Malam motata nakeso a wanke min nanda 10 minutes

    Ba sai ta cillamin key nata bah

    RAMADAN Yace kut😳

    Wlhi ina gayama sai kawai naxuba mata ido kusan na 2 minutes

    Ka katsaya kana kallona ko baka ‘daya daga cikin masu wankin ne

    Ta katsemin tunanina da fa’din hakan…..

    Kan nayi magana wanda yake goge min motar tawa Yace tab Hajjiya shima kawo tasa yayi. Baki lura da hutun da yake tare dashi bane

    Kasan dake ‘Yar iskace saita juyo da kallanta. Ayya am sorry

    Na watsa mata wani  kallo Nace Karki damu xan wanke miki aikin kai wajan kinma wucce

    Tayi Murmushi Tace ba qarya ka ha’du ga muryarka tayimin da’di Sosai dama kana tare dani dana saka agaba dan kawai nadinga jin kalmominka…..

    Kan na bata amsa yaran ya gama gogemin tawa

    Saina bata kina Nace taje ta aiwatar da ‘quxirinta xan kawo mata tata motar har gidansu

    Tayi dariyar jin da’di toh Nagode Sosai Allah ya saka

    toh bara namaka kwatancan gidanmu…….

    Na katseta da fa’din bana buqatar sani dan inaso in baki mamaki wajan kawo miki gidanku batare dakin gayamin bah

    Baka fah sani ba

    Nace karta damu

    Haka tatafi da motata tabarmin akwalar tata

    Kasan yanxu damuwata bansan gidansu bah

     kuma kamar xuciyata takamu dasanta

    Dan Wlhi yau nakasa fahimtar Komai na karatu. sai San ganinta da xuciyata dake kwa’dayin qarayi

    RAMADAN ya kalli Su SAILUBAH ka’dan Yace Auntys suna nan fah. Dan haka ka ankare.

    Sam KHAMIS ya manta Suna tare dasu

    Cikin yanayin sanyi ya kallesu Yace am sorry my Auntys

    SAILUBAH ta gallamai harara Tace ‘yan yara daku sai San mata yanxu idan aka baku su ya xakuyi dasu. Ta’ina xaku fara sarrafasu

    Ina ja muku kunne Wlhi kufita daga harkar mata dan sunfi qarfin Ku

     kubari Ku qara shekara goma nan gaba saiku nemesu

    KHAMIS da RAMADAN suka kalli juna

    Inda sabo sun saba shan fa’dan Auntyn tasu

    Cikin ‘daure fuska RAMADAN Yace toh munji

    KHAMIS Yace 20 years fah Aunty

    XEE Tace eh baku kai soyayya ba. Na roqeku kubar kula mata……

    Dai-dai nan RAMADAN yayi parking a’kofar gidansu XEE

    Tafi toh tana cewa Qawata saimun ha’du anjiman

    SAILUBAH Tace wane Kaya xamu sane aciki

    Tace eh toh musa let ‘din nan mana

    Tace red ‘din Tace eh shi

    Kana takalli KHAMIS Tace toh kuhuta samari

    Yace toh Aunty XEE sukayi gaba

    Ita mah tayi gidansu tana tunanin KHAMIS itadai tana sanshi yaran na burgeta ga iya wanka kamar RAMADAN

    Gashi hancinta baya manta qamshinsa

    Maman ta kalleta Tace ya dai naganki kina Murmushi

    Tace Wlhi mamah KHAMIS ne yake birgeni

    Tace ayya KHAMIS ai yanada hankali

    Tashige toilet tana cewa ba lefi kam

    Hakama suka sauke KHAMIS agidansu

    RAMADAN Yace karka damu abokina akwai mafuta

    KHAMIS Yace nasan bama rasata. Xan nemi FAWAS mah

    RAMADAN na parking a farfajiyar gidan nasu SAILUBAH

    Yace Auntyna

    Na ‘danga wayarki

    Tamiqa masa da ficewa daga motar tayi falansu

    Annan tatarar da Abbanta yana cin abinci Umma na gefanshi Wato matar Abban nata dake haka suke kiranta Tace sannu da gida Abba

    Yace sannu kundawo lafiya Tace lafiya lau

    Yace toh Madallah in kin gama cin abincin naki kixo kisa meni

    Gabanta ya fa’di Tace toh

    Wanka tayi ko cin abincin batayi ba taje gunsa

    Yace dama xan da’da tuna miki ne akan batun tsaida Miji

    Wlhi kika cikamin ciki xan aurar dake ga wanda naga dama

    Tace kayi hakuri Abba ka qaramin lokaci

    Yace ke kika sani nidai na qara miki lokacin

    Dan yana wuccewa baki kawomin Wanda kike so ba Wlhi kinji na rantse saidai kawai kiji Nace kitashi kibi mijinki

    SAILUBAH ta sunkuyar da kanta cikin ladabi Tace insha Allahu hakan baixai faru bah xan kawo Wanda nake so

    Yace Allah yasa jeki

    Nan Tatashi xuciyarta cike da tunani kala kala

    RAMADAN ko gidansu yayi direct yayi part ‘dinsa. Dan gidan nasu acike yake tam da mutane ‘yan biki

     yaune walimar yayarsa Saudat gobe ‘daurin Auranta

    Ya baje a gado yanata bincikar wayan SAILUBAH.

    Har yasami abinda yake nema watoh number Alhaji Jamilu Wanda SAILUBAH tayi waya dashi ‘daxo

    Nan ya kirashi ringing biyu ya ‘dauka cikin sauri yana fa’dan Allah yaja da xamaninki tauraruwa

    RAMADAN ya runtse ido Cikin kamilalliyar murya Yace ba ita bace na kiraka ne in gaya maka wani abu

    Alhaji Jamilu Yace toh ina jinka

    Yace Kasan  da cewa tarayyarka da ita haramun ne

    Dan babu kyau Nema acikin Nema

    Dan da sadakin wani akanta yanxu haka baifi watanni bane bikinta

    Cikin muryar tashin hankali Alhaji Jamilu Yace Wlhi ban san An kawo sadakinta  ba

    RAMADAN Yace toh yanxu nagaya ma danni qaninta ne

    Yace Nagode Sosai yaro Allah ya maka albarka

    RAMADAN Yace AmEEn da kashe wayan

    Sannan yayi blocking ‘din number Sa da delete ‘dinta

    RAMADAN kenan ya tsani yaga kowa da Auntyn nasa. Shiyasa yake koran mata samarinta sanranshi. Tayi fa’dan tayi maseefar Sam bayaji. Iya kacinsa da ita shine ya bata hakuri

    SAILUBAH ko daqar taci abincinta burinta tagama taje gun Qanin nata suyi shawara

    Hakako akayi. Data gama Komai saitaje tasamu kakarta Tace kakane bara naje gidansu RAMADAN

    Tace har lokacin walimar yayi ne

    SAILUBAH Tace wai walimar walimar Saudat

    Tace eh mana. Taxoma nemanki ‘daxo keda XEE wai kimata lalle ne kome tacene oho na manta

    Girgixa kai SAILUBAH tayi Tace sai qarfe hu’du walimar da sauran lokaci

    Tana fa’din hakan tafito daga falan nasu

    Tafi toh kenan idan ya sauka alungun Gidansu wata Baraka dake kusa dasu

    Saita dinga jin kamar kukan yarinya. Cikin qarfin hali tayi lungun

    Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un. Tafurta hakan da qarfi. Dan Ganin wani narkeken qatan garde a’kalla xaiyi shekaru arba’in 40 Ya danne wata yarinyar makwaf ciyarsu ‘Yar miciciya batafi shekara goma ba

    Aiko SAILUBAH me xatayi inba kurma ihu ba. tana fa’din jama’a kuxo ga wani axxalimin mutum yana San 6atama yarinya rayuwa…….

    Kan kace me😳 tuni gun ya cika da jama’a Suna tafi da Allah wadai da shi da mamakinsa

    mutumin ya saka wandansa SAILUBAH ta cukume masa riga Tace Amma kai kam Allah yayi tsinannan tsowo

    Fasiqi axxalimi me mumunar xuciya ‘dan iska

    Kalli yarinya qarama kana san 6ata mata rayuwa

    Idan iskancin kakeji mexai hana kaje gidan karuwai kayi da wacce ta dace dakai. Tunda xuciyarka tamace da son abinda Allah bayaso

    RAMADAN Wanda yafito dan rahotan da qanwarsa takai masa.

    Xuciyarsa tacika da takaicin Auntyn tashi yayi dabarai kwatan mutumin ahannunta……..

    Kan yayi magana sai gani sukayi

    Iyayan yarinyar sun rufe mutumin da duka Sosai

    Mutane na fa’din gwanda aci ubansa Suna tayasu dukansa

    SAILUBAH takai hannu xata tayasu itama…..

    RAMADAN yajah hannunta sai Gidansu

    A farfajiyar gidan yasake mata hannun nata

    Yace haba haba Auntyna meya kaiki aikata haka. Kamata yayi da kika gansa kimasa wa’axi tsakaninki dashi. Amma bai dace kitara mishi jama’a haka ba

    Tunan asiri bashi da kyau ai

    cikin maseefa ta hayyaqu miki tace banyi hakan da kaso ba.

    Irin sune ‘yan iskan da in ba haka akayi musu bah baxasu dena abinda suke ba

    Yace toh wai ke ina ruwanki meya shafeki kawai kinje kintara jama’a maxa da mata kowa yana kallanki harda wani kai hannunki jikin qaxamin mutumin. kin dai kwafsa kawai kiyarda da hakan

    Yafa’da kamar xai rufeta da duka

    Tace baxan yarda da hakan ba

    danni abindayi dai-dai ne

    Kana maganar abarsa ya6ata mata rayuwa kenan ko

    dan ba kasan xafi da ra’da’din da iyayanta xasu shiba

    Tafa’di hakan dasan ficcewa daga gidan

    Yayi saurin kamo hannunta dan yafi kowa saninta sarai yanxu xata qara hurama wutar fetir .

    Cikin sanyin Murya Yace toh yi hakuri Auntyna gwara da Allah yasa kika gansa

    muje im baki wayanki pls👏🏻

    Ta’daure fuska xata kawo mishi matsala yayi saurin janta part ‘dinsa

    ‘Yan biki suka saki baki Suna kallansu har sanda suka qule Sannan suka cigaba da har karsu Suna tuno ‘Yar cacar bakin nasu

    San da ta xauna kan kujera. Cikin lallami Yace am sorry Auntyna bana san 6acin ran nan naki.

    pls ki temaken Kisake min fuskarki ko nasamu nutsuwa araina dan Allah

    Ta harareshi dayin  kwafah.

    Ya marairaice mata tamkar xaiyi kuka

    Tace najini dan Allah

    Sai kace wani yayana ka wani rufeni da fa’da wai na kwafsa……

    Saurin rufe mata baki yayi da hannunsa…..

    Xirrrrr taji

    Ita dai akowane lokaci idan RAMADAN ya ta6ata saita tsinci kanta cikin wani hali kome yasa oho

    Yace ina miki addu’ar Allah yabaki miji me ha’kuri da halinki Auntyna

    Da Takaici Tace AmEEn. Wai kai baka jin wani abune idan ka ta6ani

    Ya ‘danyi jim can ya ta6e baki Yace banajin Komai

    Tajah tsaki ako wane lokaci ka riqeni jin xirrr nakeji tun daga Kaina har babban ‘danya tsana

    Yayi Murmushi da qara kama hannunta Yace qila ko danni Yarone.

    Tace ko

    Yace ba mamaki

    Kasan miye matsalata

    Ya girgixa mata kai alamar aa da kuma kafeta da ido

    Wlhi Abba ne yaqara min tuni akan Aurena

    Yace toh miye

    Tace da matsala mana

    Yace ba wani matsala kawai kifitoh da wanda ya kwanta miki arai

    Ta gallamai harara

    Kana barina ne da samari

    Da xakace in fito da wanda ya kwanta min arai

    Yayi murmushin jin da’di tare da murxa hannunta cikin wani salo Yace xan soki da qaramin yaro

    Cikin ‘daure fuska Tace dawa kake….

    Kan ya bata amsa taci gaba wajan fa’din. Kafi kowa sanin tsarina da ra’ayina bana san naqara jin wannan kalmar daga bakinka

    Ina ganin xan janyo Alhaji jamilu jikina musaba kaga sai kawai na gabatar dashi matsayin mijina ko

    tunda ya ha’du

    Murmushi RAMADAN yayi Yace duk da ban gansa ba Amma hankalina ya kwanta dashi kifito dashi ‘din kawai

    Ta sauke ajiyar xuciya xatayi magana wayarsa tafara ringing…….

    Sake hannunta yayi ya duba wayar

    Amina ya gani

    meenat ya akayine

    Tace lpy lau my luv

    Yanxu haka ina kwance a gado naci kwalliya Sosai dan xuciyata tacika dasan ganinka muje shan iska. Allah yasa baka manta bah

    Ya dafe goshi cikin marairai cewa Yace am sorry farin ciki na

    Naso in cika miki alqawarin danayi miki Amma kaxai yuhuba

    Xanso kiqara bani dama akaro na biyar

    Amina taja numfashi cikin rashin jin da’di Tace Ashe kana sane ba yau kasaba yimin hakan ba. Da gaske yau shine karo na biyar………

    Wani shegen tsaki SAILUBAH tajah da gallama RAMADAN harara

    Yayi Murmushi da tsaida idanshi akan le6anta

    Cikin sauri Yace eh kimin hakuri ina da wani babban uxiri ne xan kira pls

    Yana fa’din haka ya kashe wayan batare da Yaji cewarta bah

    Kamar yanda lamarin yasa ba faruwa mishi hakance tasake faruwa SAILUBAH taqara kai mishi harara Tace Wato kai baxaka fita aharkar mata bako

    Qanqanin yaro dakai Kasan kadinga yaudarar mata ko

    RAMADAN ya xuba mata ido da fa’dawa tunin wai sai yau she ne Auntyn tashi xata dena kiransa da yaro

    Da ‘daure fuska Yace shekarata ishirin xaki dinga kirana qaramin yaro

    Haba dan Allah yanxu inda agaban budurwar tawace shikeban kinsa tarainani dan Allah kidena kirana qaramin yaro

    Tayi dariya dan ganin yanda yayi kicin kicin da fuska tunba yau ba

     tasan RAMADAN baya san  araina shi shiyasa yake ganawa Khairat axama qanwarshi dan baqaramin tsoranshi take ba

    Gashi dasan girma Sam baya SO ace wane ya girmeshi

    Ita ka’daice xatace mishi qaramin yaro baxai CE mata Komai ba. Toh yau gashi yayi kicin kicin da fuska

    Tashi tayi taje gabansa ta manna masa kiss a kumatu kamar yanda tasaba yimai idan ta 6atamai rai Tace sorry ‘dan Qanina kai Babban yarone

    Xaka kaimu walimar Saudat kajiramu.

    Yace aa

    Dan Allah

    To naji

    Tatashi xata fita Yace Auntyna yunwa nakeji

    Tace toh bara na kawo maka abinci. Tafita

    Yabita da kallo

    Bata ‘dauki lokaci ba sai gata da plate da drink ahannunta

    Tadiremai a gabansa

    Taliyace Momy tayima Dady dakai ‘daxo

    Yafara ci yana cewa idan baku shirya da wuri bah tafiyata xanyi

    tashi tayi da ‘daukar wayarta tana cewa bara nagama Amaryar

    Ka’dan yaci ya kora da drink kana yayi wanka Cikin qananan Kaya yakira FAWAS da cemai Su ha’du a gidansu KHAMIS dan shi KHAMIS ‘din yayi wani banxan kamu. Yace OK

    Tunda ya fitoh qawayan Amarya yayar tasa suke kallansa

    Cikin maseefar sha’awarsa dan yayi kyau Sosai ya fitoh a bature sak

    Dan yanayin shigar tasa sai qamshi yake

    Ya shiga falan Momy nashi annan yaga SAILUBAH tanata xuba cikin sanyayyiyar muryarta

    Tanajin qamshin turaransa taja numfashi da lumshe

    Yace momy ina xuwa yanxu

    Tace da fatan kaci abincin da yawa Yace eh. da maida kallansa ga SAILUBAH Yace Auntyna bara inje yanxu xan dawo

    Ta shagwa6e fuska Tace pls karka shanyamu Yace Karki damu my Aunty. Yafita da sauri hotan fuskarta na manne cikin kwayar idansa yana hango shagwa6ar tata

    ‘Yan matan suka bashi da kallo dan shi’din yayi

    Wata Salma Tace nikam ina san yaran nan SAILUBAH….

    Harira ta katseta da fa’din ai yayine tako ta ina

    Saudat Tace ai shegen yarone yasan kan Komai daya dace dashi.

    Haka kowa Yata fa’dar albarkacin bakinsa akan RAMADAN

    SAILUBAH tayi shuru kawai tana jinsu

    Ashe har qawayan Momyn nashi sunyaba da shi

    Shiko yana fitowa daga gidan nasu idan shi ya sauka akan Jamila

    Wato Jamila wata ‘Yar unguwarsu CE tana MASEEFAR son RAMADAN

    Tarigada tasan duk wani motsinsa dan haka kanya fitoh daga gida take kafawa ta tsare akan wani dakali da yake fuskanta gidan nasu. Tun baya ganewa har ya ganota suka fara gaisawa

    Yafara sakar mata da kalamai. Shikenan fah ya hargitsa mata tunaninta

    Kowa yasan soyayya suke

    Ya sakar mata Murmushi cikin sanyin murya Yace Jamis tauraruwata yau baxa abari naxo bane

    0 Comments

    Heads up! Your comment will be invisible to other guests and subscribers (except for replies), including you after a grace period.
    Note
    error: Content is protected !!