Search
You have no alerts.

    Riqqon Kaka Chapter 5

    RIKON KAKA

    CHAPTER5

    zaka siyar mawa, to ban siye, ka bani kudina

    kawai”. ‘

    Sunan qanwarsa da ya ambata shiya bugewa

    Abubakar ‘dukkanin gaBoBin jiki, jikinsa a sanyaye

    ya sa hannu ya Ciro kudin a gaban aljihunsa ya

    mika masa.

    Ya amsa yana fadar, “Mutanen banza kawai gaku

    Musulmai amma kuna aikata aikin kafurai,

    marasa tsoron Allah kawai”.

    Abubakar dai bai tanka, masa ba. har ya fice

    banda zafi da:. Kuna babu abinda zUciyarsa keyi,

    yaji ya tsani ragon, bai son ma gaminsa

    Yajasa ya fita waje ya sa

    yaro yai masa sallama da makwabcin su malam

    Bala talaka ne . Yana fitowa suka gaisa da

    Abubakar sannan ya ce

    ‘ “Baba, dama ragona ne zai gaza, nasan kana

    jinmu ma wata kila jiya. To shine na yanka, yau

    na kira mahauci ya taya min shi yanda nake jin

    ba zan iya siyarWa ba, gara ma na ba da shi

    sadaka na San ladan tawa tana

    wurin Ubangiji tunda mu ma za muyi layya shi

    yasa na ce bari inzo in maka magana ka aika a

    dauko maka”.

    Malam bala ya shiga godiya yana zabgawa

    Abubakar addu’a, shi dai bai ce komai ba ya

    wucc ya koma gida, Malam Lado ya turo yara

    suka daukar masa ragon.

    Abubakar ya dauki buhun ya maidawa

    Kaka, ya ce ”Ga buhun ki”. Kaka ta ce ,”Yo ya

    fasa fedewar ne?” Abubakar ya ce, “Hmm! Idan

    kun bari ba Kaka ta ce, “Kamar yaya kuma in

    mun bari?” Ya ce, “Kamar yanda kika kitsa mata

    taje ta sanar da mahaucin mushe ne na yanka”.

    Kaka ta dauki Salati da sallallami, kafin

    Ta hau rantse-rantsen ba ita tasa ta ba”. Ta ce

    “Ke Jika, wannan kuma wacce dabi’a ce za ki

    tsiro mana da ita ne?”

    Abubakar ya ce, “Wadda ki ka’ koya mata, duk

    abinda fitinanniyar yarinyar nan ke

    Keyi kaka daurin gindinki ne take samu. Amma ba

    komai, ni nasan maganinta, ba zai yiwu yarinyar

    nan ta sangarce ta lalace ba, tunda har ta iya

    wannan gaba ban san abinda zata yi ba, idan ta

    Kara girma a haka to abin kuma sai yafi haka.

    Don haka makarantar boko zan saka ta, taje can

    ta koyi tarbiyya”.

    Kaka da dauki Sallallami, “Wa za ka kai

    makarantar Abubakar? Jikar? Baka isa ba,

    wallahi babu inda za ka kaita a lalata marainiyar

    Allah. Ka kai ta makaranlar boko ta koyi tarbiyya

    k0 ta koyo iskanci?” Abubakar ya ce,”‘Oho dai, ni

    dai na fada miki, k0 kina so k0 ba kya so sai na

    kaita”. .

    ‘ Ya juya ranshi na suya ya ’bar‘ dakin, . yana jin

    Kaka na rantse-rantsen babu me kai mata jika

    makaranta.

    Anci sallah lafiya, Kaka tayi layya ta

    yanka dan marakinta, Abubakar bai yi ba don

    gaba daya ya sai da ragunan sa,. ya ce kuma ya

    gama kiwon.

    Jika kuwa kayan Naira biyar bai siya mata ba,

    haka tai sallar da tsofafin kayan ta, shi ya saka

    ma ko kofar gida bata leqa ba _ Ana gama hutun

    sallah Abubakar ya je yai wa Rukayya takardar;

    haihuwa, washegari ranar Monday tun da sanyin

    saflya ya sa tai wanka ta sauya kayan jikinta,

    sannan ya tisa ta gaba suka tafi.

    Kaka tace, “Wai gidan uban wa zaka kaita ne

    Habu? Na fada maka kar ka sake ka kaita

    makarantar bokon nan, ban son ta”. Abubakar ya

    ce, ”Ai ko sai dai kar ki so . ta, amma makaranta

    na kaita na gama”.

    Ta sa kuka, yana jinta ya tisa‘ Rukayya gaba

    suka ficce, can tsakiyar garin makarantar take

    Sha ruwa Primary School, suka dauke-ta aka

    kaita a‘ji uku, saboda ta wuce dauka.

    Suna dawowa yaje ya yanko mata (uniform) ya

    sai mata jakar makaranla da takalmi, sannan ya

    sai mata littattafai.

    . washe gari da kanshi ya tayar da ita ta: shirya

    ya tisa ta gaba har kofar

    makarantar, ya bata Naira ishirin kudin tara;

    sannan ya wuce wurin aikinsa.

    Rukayya ‘yan makaranta, karfe sha biyu aka taso

    su daga makarantar, amma idan ka ganta ba

    zaka ce ita ce tajc makarantar da sabbin kaya ba,

    tai musu budu-budu, farar abayar har ta fita

    daga kamannin ta.

    ‘Tana dawowa gida ta fada jikin kaka tana

    murna, Kaka ta ce

    “Oh Jika da tsiya dai Habu sai daya kai ki

    makarantar nan don yasan ba yanda zan yiko?”

    Rukayya ta ce “Kuma Kaka sai da aka buge

    ni, dubi baya na”.

    Ta cire abayar ta nuna mata, wurin yayi

    ,rudu-rudu da zanen bulala.

    ‘ Kaka ta ce, ”Wane dan iskan marar imanin ne

    yai miki wannan dukan? Shi yasa na ga fuskar ki

    ‘ da zanen hawaye”. Rukayya ta ce “Wani malami

    ne, wai daga muna fada ya ka mani yai ta bugu

    ni kadai”.

    ‘ Kaka ta ce, ”Matsiyaci, ya kama ki yai ta duka,

    to Allah Ya isa, tsinanne lnsha Allah bai gamawa

    lafiya, kawai ka kama ‘yar marainiyar

    Allah kai ta bugu kumar ka sami mandiri. Bari

    Habu din ya dawo Jika, wallahi ba ki komawa

    makarantar, sai dai yai duk abinda zaiyi, dauko

    furar ki gata can ki sha”.

    Rukayya ta mike ta dauko kwanon furar tana sha,

    ta ce. _

    “Kuma Kaka har Turanci aka koya mana da waka,

    amma wai (This is a boll, These is our Apple,

    That is your watch)”.

    Kaka ta tintsire da dariya har saida sashinta ya

    fito saboda bakin ba haqora, ta ce. ‘

    “Kai amma abun da dadi, duk can aka koya

    maku?“ ‘ Rukayya ta ce, “Eh Kaka”.

    Ta cc, “Ai don dai azzalumin mutumin nan da kin

    Kara zuwa”.

    . . Rukayya tace. “Ai ban Kara zuwa nima tunda

    buguna ake”. . Da yamma likis Abubakar ya dawo

    gidan .ya iske Rukayya da kayan makarantar duk

    ta: musu duwan-duwan, takaici ya cika Shi

    Duk inda wata qazamar yarinya ta kai rukayyah

    Tafita: Kazanta , daga cikin abubuwan da sukesa

    yake qara tsanarta.

    Ya watsa mata idanu babu sauqi a fuskarshi,yace

    ‘Wuce kije ki cire kayan ki kawo su wurin maguji’.

    Ta mike a tsorace

    ta nufi dakin nasu’.

    Ya tsai da ita, ‘Tsaya ki tattaro dukkanin kayan

    daudarki kawomani’.

    Rukayya ta daga kai

    Ta shige dakin, shi kuma ya wuce Washegari

    yana tashi ya nufi dakin Kaka ya tashi rukayyah

    tai shirin makaranta

    Kaka tace kai babu inda zataje donka jini nan jiya

    suka kamata sukaita bugu kamar jaka don haka

    bata komawa

    Abubakar yace,’ldanta zauna nan me zatai miki?

    Nan makarantar allo ce kikai kane kane kika

    hanata zuwa wao bugunta ake , sannan kuma

    itama makarantar bokon sai ki

    hana? To wallahi .ko kasheta za a rinka yi tana

    dawowa sai taje har makarantar allon sai ta

    koma“.

    Kaka ta ce “Tunda dama ba qaunar ta kake ba ai

    dole ka kaita inda za a kashe ta saboda

    mugunta, haka kawai ka dauki karan tsana ka

    dorawa yarinya, ka kaita a kashe ta don Allah,

    idan an tashi a aiko mani da kai da qafarta gida”.

    Abubakar ya finciko Rukayyar dake kan gado ya

    jata suka nufi kofa YANA FADAR. ’

    ”Ba za, a kashe taba amma fa za ta daku kamar

    ikon Allah”.

    Bai ji abinda take fada ba don har ya kai bakin

    kewaye, ya zuba mata ruwa a bokiti ya bata ta

    shiga wanka.

    Tana fitowa ya mika mata kayan makarantar ta

    saka, ya ba ta mai ta murza ya zaro Naira

    hamsin ya bata, ya ce.

    Maza ki wuce ki tafi, kuma zan biyo bayanki

    yanzu, ki tsaya wasa k0 da labe ne kiga ‘ yanda

    zanyi da ke. Kina dawowa daga

    makaranta ki ka ci abinci ki ka hula, ana kiran

    sallar azahar kiyi sallah ki wucc makarantar allo

    idan ba haka ba wallahi kika bari na samu labarin

    baki zuwa na lahira sai ya fiki jin dadi wuce ki

    tafi. ‘ Simi-simi ta wuce, daga daki Kaka tace.

    ”Yanzu baka barin tai kalaci haka za~ ta wuce ta

    tafi?” , Ya‘ce, “Bata yi, ga Naira hamsin nan na .

    bata ta siyi abinci ta ci”. ‘ -Kaka tace, “Indai

    mugunta ce irin taka ai ta wucc da haka Habu,

    yanzu haka zaka kora , min ita bata ci komai ba

    salon tai karo da mayya k0 maye su lashe mini

    ita?” » ‘ Abubakar ya e, ”Su hadiye ta idan ta

    tafi”. ‘ , “ ” Kaka ta cc, ”Ba bakin ka ba, me

    mugun baki. Insha Allahu aniyar ka sai ta bika”. .

    Bai tanka mata ba ya wucc dakinsa yai nasa

    shirin ya fice ya tafi wurin aikin sa, amma ‘yana

    can sai da aka kawo mashi kashcdi wai Rukayya

    tayi fada da wani yaro har ta cije shi a hannu ya

    fasa. Ya basu hawuri sannan yaje

    “Tana dawowa daga makarantar tana hutawa

    akai sallar azahar ta fito zata tafi makarantar

    allo

    Kaka tace, ‘Yanzu zuwa za: kiyi k0? Mugun yaron

    nan ya hanaki zama lafiya, duk indayasan za a

    zalunceki saiya turaki Allah Ya saka miki’. .

    Jika

    Haka ta wuce makaran allon,.a can sukai sallar

    la‘asar, Sai biyar na yamma aka tasosu

    Tana dawowa tasamu Abubakar na gyaran cefane

    cefane ta giftashi zata wuce ya ce‘

    .. ’Kezonan’. , ta dawo gabansa ta durkusa ya

    dubeta sosai kafin yace ,‘Wato saboda bakeke

    wankinba shi ,yasa idan kika dawo makarantar

    baki canja kayan sune na zaman gida kuma sune

    na

    Yawo cikin gari ko?‘

    Shiru ba amsa, ya ce “Tashi kije ki ciri kayan ki

    kawo mani”.

    Haka ta mike ta ciro ta dawo da su a hannu, ya

    ce

    “Dauki bokiti gaya can da ruwa kisa ki wanke”.

    Gaban‘ta ya fadi don tundatake bata taba wanki

    ba, shi ke yi mata da kanshi. Haka ‘ ta mike taje

    ta soma wankin kayan, yana kallonta har ta

    gama ya amsa ya shanya. . .. ’ Sannan ya ce “ki

    wanke hannunki ki , xo ki yanka mani alayyahun

    can da albasa”. ‘ Rukayya ta dubi hannun nata

    babu abinda ya yi amma har sai ta wanke ya ce.

    ‘ “K0 baki ji ba?”

    , Haka ta wucc ta dauki buta ta wanke hannun

    nata sannan ta je ta zauna tana yankan

    alayyahun ya dora sanwar taliyar sa,tana gama

    yankan alaiyahun ya ce

    Jeki ki zuba” Ta tafi zata zuba cikin tukunyar .yai

    saurin daka mata tsawa.

    ‘ “Ke banza, haka za ki zuba shi? Barbada mashi

    gishin’ ki sa ruwa ki wanke”. ’

    ‘ Ta dauki uban gishiri ta maka yana kallonta ya.

    ja tsaki ta zuba ruwa ta wanke ta tsane shi

    sannan ya ce ‘

    “Je ki zuba”. ‘ “

    Taje ta zuba ta rufe, ta dawo gabansa.

    “Na gama”.

    Ya ce, “Jeki shi kenan”.

    take ta nufl daki don kar ya qara saka ta wani

    aikin

    *** ******* ***

    Wata ranar Juma’a RuKayya tana . makaranta tai

    fada da (monitor) din ajinsu wai ta rubuta

    sunanta cikin ‘yan surutu, malamin ya buge

    su.duka Shine fA yana fita ta ‘ kama monitar da

    kokawa’ gata ba iya fada tai ‘ ba, tai mata, duka

    sosai. Akaje aka fadawa ‘ (headmaster) yazo da

    kansa da bulalar sa ya zane Rukayya: radau har

    tai fitsari saboda .

    .azaba.

    Yana fita ta dauki jikkarta ta gudo gida tana

    kuka, ta fadawa Kaka. Ta ce, “Ai k0 yau sai ya

    san ya debowa

    kansa masifa”.

    Ta dauki mayafinta ta ce “Muje inga matsiyaci”. ‘

    Ta ja gida ta rufe suka dauki hanyar

    makarantar har office dinsa ta kaita, yana

    zaune saman kujerar dake gaban teburinsa sai .

    wani mutum dake daga can gefe suna

    magana. ‘

    Kaka ta sawo kai cikin office din ba k0 sallama,

    ta dubi mutumin dske saman _kujerar gefe tace. ‘

    “Malam wurinka nazo, zuwa nayi inji uban da

    yasa ka sa bulala ka rinka laftar mani

    jika kamar ka samu jakka, k0 k0 shi Habu din

    ‘ nc da ya kawo ta ya ce ka sa bulala kai ta

    bugunta harta ‘fita hayyacinta tai fitsari? To kotu

    zata rabani da kai, wallahi sai nayi shari’a da kai,

    sai ka bani labarin dalilin bugar mani ‘ya babu

    gaira babu dalili”.

    Mutumin yace Yi hakuri baiwar Allah, bani ne

    (headmaster) din ba, gashi nan, nima zuwa nayi“.

    Ta ce, “Karka sake ka zage ni’da turanci wallahi

    na gaya maka, nima ina da

    jika kamar ka dan makaranta” ~ Saurayin ya ce,

    “Ikon Allah, yi hakuri don Allah Hajiya” ‘ ‘

    Ya mike ya bawa (headmaster) hannu sukai

    musabiha, ya ce.

    “Ni zan wuce Yallabai, zan kira ka a waya k0 mi

    kenan”. _ Ya wuce abinsa ya bar (headmaster) da

    rigima. ‘ . Da yake kwararren dan boko ne sai ya

    mike daga kan kujerar da yake ya ce.

    “Hajiya zauna, bisimillah sannu da

    _ zuwa, bari akawo miki lemu”. Kaka ta zauna

    tana fadar, “Karka kaWO mani komi, dan iskan da

    ya bugi Jika kawai

    nake nema, wallahi sai na rama mata ,kaji na

    fada maka

    Lol ran kakafa ya baci mai zai biyo baya mu tara

    later

    a zallah shared a profile .

    0 Comments

    Heads up! Your comment will be invisible to other guests and subscribers (except for replies), including you after a grace period.
    Note
    error: Content is protected !!