Search
You have no alerts.

    Riqqon Kaka Chapter 3

    RIKON KAKA

    CHAPTER3

    Kaka tace”Ba kowa, zaluncine kawai da kuma ba

    ya qaunar . ki” Rukayyah tace “Ai nima shi yasa

    bana Raunar sa, dama ya mutu

    ~ Kaka tace”Idan ya mutu ai muma da mun

    mutu, don da Allah muka dogara da shi muka

    dogara, idan ya mum jika ai sai munyi bara“

    ‘Rukayya ta diro daga kan gadoh ta , dauko kofi

    ta zuba furar da kaka ta gama damawa, sannan

    ta koma bakin gado ta soma sha. *

    _ Kaka ta mike ta kuskure bakinta saboda kiran

    sallar la’asar da aka fara a masallaci.

    Misalin karfe biyar dai-dai taiwa Abubakar a Kofar

    gida, a gajiye liqis ya dawo gidan tamkar Wanda

    aka bawa kashi. Ya cire kayan jikinsa ya fito ya

    :nufi kewayrn gidan ya watsa ruwa ya dawo

    ya‘saka ‘yan Kananan kaya mararsa nauyi,

    sannan ya fito tsakar gidan ya

    nufi dakin kaka.

    Tana kwance tana hutawar ta sai jika ce keta

    faman * ‘ wasan kyallaye, tana ganin Abubakar

    gabanta ya fadi, ta shiga faman raba idanuwa.

    Abubakar ya tsaya bakin kofar dakin ya watsa

    mata harara, kafin yace

    “Naga ranar da zakiyu hankali, qatuwa dake kin

    tile kina wasan kyalle. Mtsw! Allah wadaran naka

    ya lalace’. .

    Kaka tai saurin tashi zaune, “Ah! Ka dawo kcnan

    k0, sarkin mita uban ‘yan iyayi?”

    Ya cc, ”Ni ba mita nazo ki min ba’“.

    Ya wurgawa Rukayya Naira hamsin, yace

    “Tashi maza kiyo min cefane wurin Haladu in

    dora sanwa, kuma saura idan kin tafi kije ki ta

    neme-nemen fitina”.

    Ya juya ya barsu ya nufi wurin murhu ya hada

    itatuwa ya dora sanwar wake, sannan ya koma

    dakinsa ya kunna kallo a wayar sa

    Rukayya ta tafi siycn cefanen tanata faman

    dirc~dircn ta a hanya, tana shawo kwanar

    Rukayya ta rinqa krta musu dariya har tana

    dukawa ta zub da sauran duwatsun ta nufi gida

    tana tsallen murna.

    Ta kawo masa cefanen dakinsa, a lokacin ta

    tsaya daga bakin kofa.

    “Ga cefanen”.

    Yai kamar bai ji ta ba, sai da ta mai maita wurin

    sau uku sannan ya mike yazo ya amsa tamkar

    wanda ya rike wani abin kyama, yana binta da

    kallon kyama

    Duk tai dagaje-dagaje da ita, kayan nan duk

    sunyi dauda, ita kanta fatar jikinta taji jiki. Har

    zata wuce yace.

    “Ke, zo nan.

    Ta dawo, “Gani“.

    Kamar ba zai tanka ba. can kuma ya dame ya ce

    ”Yaushe rabon da kiyi wanka?” Shiru ba amsa, ya

    daka mata tsawa koba dake nake bane

    Tace; “Nima na manta

    Abubakar ya girgixa kai wuce kije ki ciro kayan

    jikin da sauran

    daudar ki kawo min a bakin maguji, kije ki debi

    ruwa kiyi wanka, sakarya, qazamar Wofi. Wuce ki

    tafi

    Da hanzarintata wuce, .ya rufa mata baya. Haka

    kawaiyake jin tsanar yarinyar a. ransa saboda

    qazantar ta da kuma‘ kin jinta kamar _ wadda

    aka kadawa da ruwan sanyi. ., ’

    Ya wanke cefanen ya zuba a turmi yana

    jajjagawa, Rukayya ta debo kayan ta kai masa a

    bakin maguji ta ajiye masa tuli guda, sannanta

    debi ruwa a bokiti ta nufi kewaye tai wanka, ta

    wuce daki. ‘

    Kaka ta cc, “Da yake shi ne ai gashi nan kinyi

    wankan,anfi sati ina matsa miki da kiyi wankan

    amman kin kiya sbd kin rainani

    Rukayya ta xumBuro baki, ta janyo jakar kayanta

    ta fito da wata cukurkudaddiyar

    doguwar riga ta saka, bata shafa mai ba balle

    hoda, tai zamanta abinta.

    ‘ K0 kadan Rukayya bata son kwalliya,

    Bata ma damu da tsaftar jikinta ba ballantana

    wata kwalliya. .

    Kaka tace, “Ki dauko k0 mai :neki murza Jika, kin

    zauna da jiki haka furu-furu”.

    Ta zumBuro baki tai kwanciyar ta hankalin ta a

    kwance

    Abubakar yai jalof din shinkafa da wake,

    yana kammala sallar magariba ya filo ya ,dibi

    nashi ‘abincin ya kwashe masu sauran ya kai

    masu sannan ya wuce dakinsa. Washe gari .

    tunda sanyin safiya Abubakar ya gama jidar ruwa

    sannan ya ta da Rukayya ta nemo masa tsari, ta

    zunguro baki‘ alamar bata so ba, ta dauki bokitin.

    Abubakar na kallonta cike da takaici, ya. danne

    zuciyar sa ya kyale ta. “

    Gida biyu ta shiga ta samo tsarin ta nufo ~gida,

    tana cikin tafiya ta hadu da Zulai da Rakiya, bata

    kula su ba saboda tsarin da ta debo. Abokanen

    fadanta ne sosai suma ‘yan neman rigima ne

    Zulai ta bangaje ta har bukitin tsarin ya fado

    daga kanta ya zube bokitin ya fashe.

    Rukayya ta ce, “Kaikai! Ni ku ka fasawa bokiti?

    Wallahi ba zan yarda ba

    Sukace “An zubar, k0 akwai abinda za kiyi?“

    Ba ta tsaya mai da masu magana ba ta cakumi

    Zulai da kokawa, ta yarbar da ita a cikin tsarin

    tana duka, ganin haka yasa Rakiya ta shiga

    dukan Rukayya, suka tararmata su biyu, sai da

    Allah Ya kawo wani mutum sannan ya raba su.

    ‘ Rukayya ta dauki fashasshen bokitin tsarin ta

    nufi gida tana kuka, Abukabar na ‘shara a tsakar

    gida yaji kukan ta, ya mike da tsinsiya a hannun

    sa yana jiran shigowar ta.

    Bai ,yi mamakin ganinta da fashasshen bokiti ba,

    jikinta duk tsari da qasa. Wani irin bakin ciki ya

    turnike mashi zuciya, yai tsaye yana kallonta. Ta

    kasa motsawa daga inda take,

    tai tsaye tana rera masa kuka. Kaka tai saurin

    hankado labule

    tana fadan ‘ ”Mugu, dukan nata din kake k0?

    Indai ka

    kashe ta Habu ka huta

    Ganinta da tayi tsaye da tsari duk jikinta yasa tai

    saurin nufarta tana fadar. ‘

    Jika, wane la’anannen ne yai miki haka? Lahaula

    wala quwata, kashe ki ake so ayi ne Jika? Wai

    me ki kaiwa mutane ne yasa basa kaunar ki?”

    Sai tasa kuka har da hawayen ta, cikin kuka tace

    Waye yai miki haka Jika?” Rukayya ta ce, ”Su

    Rakiya ne da Zulai’. * Kaka ta ce, ”Ai ko yau sai

    na rama miki, don wallahi basu bugi banza ba”.

    Abubakar ya qaraso yana fadar, ”Allah Yasa kije

    su hada da ke ai ni zuciyata fari ta Allah Ya qara,

    ai da ana miki haka da kin rage wani iskancin da

    kike wa jama’a”. Kaka ta ce ”Tunda dama ba

    tausayine dakaiba Ai idan sun kashcta baka da

    asara, ai ni nasan ba qaunar mu kakc ba”dama.

    Ta juya ta janyo zani ta yafa ta nufi hanyar fita,

    Abubakar ya ce ‘ ‘ “Ina zaki kuma?”

    “Zuwa zanyi in ramo mata tunda

    Kai baka da amfani. Na lura ai na lura matsoracin

    , banza nekai, baka da fushi sai cikin gida”,

    Tayi waje tana mita ganin, bai ce mata Kala ba

    har ta fice. Ya dubi Rukayya dake kokarin binta,

    ya daka mata tsawa

    “Karki kuskura , munafukar banza, duk wata

    masifa ke ke haddasa ta, kinja ana ta zagar

    mana kaka, kuma duk saboda ke. In bacin keda

    kr debo mana rigima da wa ma yasan damu?

    Masifaffiyar yarinya kawai.

    Sai ki wuce kije ki cire kayan kiyi wanka ki canza

    wasu, aike ne tunda baki so daga yau an gama

    aikcn ki, sai ki zauna”, Ya watsa mata harara ya

    wuce abinsa. .

    Ta wuce simi-simi ta dauko zani ta debi ruwa ta

    nufi krwaye tai wanka, ta dauro zanin ’ ta ajiye

    mashi masu tsarin a bakin maguji, ta wuce daki

    ta canza‘ wasu kayan. Sai dai babu mai ba

    kwalli, haka aka sa kayan ta kama tai kwanciyar

    ta saman gudo.

    0 Comments

    Heads up! Your comment will be invisible to other guests and subscribers (except for replies), including you after a grace period.
    Note
    error: Content is protected !!