GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 03
Ido suka hada da bibi,dukkansu sai aka rasa me cewa dan uwansa wani abu,duk kuwa da cewa alamu sun nuna kowanne bakinsa cike yake fal da maganganu.
Qarasowa bibi tayi ta zauna tana duban ama,ba tare data buqata ba ama ta sulale ta zauna aqasa tana duban bibi
“Har yanzu kunqi yimin cikakken bayanin meye maina ya yiwa sultana?”
“Ya karbi budurcinta ne bibi ta qarfin tsiya” ama ta amsa mata kai tsaye kanta a qasa tana me matuqar jin nauyin bibi din,don babu magana kwatankwacin hakan data taba ratsawa a tsakaninsu,uwa uba babu wani buqatar ci gaba da boyewa bibi din,don kuwa me afkuwa ta riga data afku.
Dif bibi tayi tana juya abun cikin ranta,duk da ta riga ta gama hasashen komai cikin ranta da zuciyarta
“Bansan da wanne baki zan fara neman gafararki ba bibi….” Katseta bibi din tayi ta hanyar daga mata hannu
“Daga haidar har sultana waye bare?,waye zan ware nace ba nawa bane hamdiyya?” Ta fada da wani irin tune na sarewa da sanyin gwiwa
“Ni babu abinda zancewa da ubangiji na saidai ALHAMDULILLAH har da ya haskamin,ya kuma hanani nutsuwa sai dana tabbatar na maida sultana halalinsa. Yau inda ace ita din ba halalinsa bace ya aikata mata hakan nayi imanin zuwa yanzu wala’alla ina kushewata……saidai duk da hakan…….” Ta fadi daga qarshe muryarta na karyewa da wani irin yanayi
“Duk da hakan abinda yayin banbancinsu kadan da fyaden bibi……sultana nawa take bibi?,duka duka shekarunta nawa?,a musulunce ya kamata a nufeta a haka?,bibi……. kinsan dinki nawa aka……” kasa qarasa tayi saboda yadda zuciyarta ta karye hawaye ya sake tsargo mata a karo na biyu.
“Akul……kul kika sake bari hawayenki ya fita akan wannan batun,idan ba haka ba zamuyi mugun samun sabani ni dake,kin manta masifar hawayen uwa akan d’anta?” Bibi ta gada a hargitse kuma cikin gigicewa.
Ba aliyyu takewa kuka ba sam sam sam, a’ah tana tuna girma da masifar zafin stitches ne koda jikin babbar mace bare sultana da duka duka bata wuce raino ba.
Sau uku tana zirya sashen maina don ganewa idanunta ko ya shigo gidan kafin ta fita amma bataga alama ba,haka ta shirya duk wani abun buqata ta dauki daya cikin masu aikinta da driver dinta suka koma asibitin.
A hanyar komawar dai duk sammakal,tunda ta zauna cikin motar zuciyarta ta lula a tunani. Fuskar aba take hangowa kawai,har ta fito daga gidan babu wata magana data hadata da shi,ta tabbatar kuma abunne yake dukansa kamar yadda yake dukanta.
Cikin qanqanin lokaci moudu driver ya sauketa cikin asibitin. Shi ya fiddo komai da tazo dashi. Abinci ne tasa zunnira ta shirya cikin qananun warmer’s masu kyau,saboda batasan sanda sultana zata farka ba,kada ta farka cikin dare ta kuma buqaci abinci,sai kuma kayan sanyawar sultana din da wasu qananun kayan buqatu nata.
“Idan ba damuwa kaje ka shirya ka dawo,ina da buqatar ka kwana cikin asibitin tare damu,don bansan meye zai iya tasowa ba na gaggawa” tace da moudu sanda ya gama kwashe kayan tsaf ya shigar mata dasu ciki,ta furta maganar tana fiddo kyawawan qafafunta dake sanye cikin wani rufaffen takalmi maras tudu
“To ba damuwa ma’am in sha Allahu” ya amsa mata a ladabce.
Akwai taqaitar zirga zirgar jama’a sosai cikin asibitin,abinda ke alamta maka cewa lallai dare ya soma tafiya. Cikin wani irin kasala mutuwar jiki da rashin jin dadi jiki da kuma na zuci take takawa har ta isa dakin.
Ta iske qwararrun nurses biyu zaune a dakin,suna hirarsu qasa qasa ta yadda ba zata damu mara lafiya ba bare ta tadashi.
Sunfi kowa sanin ita din wacece cikin qasar nijer,don haka girmamawa ta musamman suke bata. Sannu tayi musu cikin halin sauqin kanta idan taso,suka amsa mata,sannan suka sake duba komai,kama daga file din sultana,ruwan dake shiga jikinta da sauransu suka tabbatar komai yana kan order
“Zamu wuce ma’am,duk abinda kk da buqata akwai waya da zaki kira(ta fada tana nuna mata inda wayar take a girke)”
“merci(na gode)” ama ta furta idanunta akan sultana
“c’est bon” suma suka maida mata amsa sannan suka nufi qofa suna mata sallama.
A hankali ta matsa gaban gadon tana sake dora idanunta akan fuskar sultana. Kyakkyawar baby face dinnan,wadda bata rabo da tsiwa da rashin kunya gaba daya ta canza,qaramin bakinnan da baya rabo da murgude murgude yau din gaba daya a kumbure yake. Kyawawan idanunta masu wani irin maiqo kaman an diga ruwa a yau din ba sosai kake hangosu ba saboda kumburin da gefansu yayi. Wani abu taji ya motsa zuciyarta,karo na babu adadi taji abun ya sake taba zuciyarta sosai. Inda ace saddi mace ne kwance haka cikin wannan halin wani d’a namiji yayi masa haka ya zataji?. Tambayar data sanyata jawo kujera ta zauna sosai gaban gadon tana ci gaba da kallon fuskartq zuciyarta kuma na hakaito mata yadda abun ya gudana tsakaninsu,wani nauyi na sake sauka mata a qirji. Fuskar nafessa take hangowa
“Ya rabbbb…..kada ka kamani da laifin gudun qaddarar da nayi,ya ilaheee ASTAGFIRUKA” ta furta a fili saidai can qasa hawaye suna cika idanuwanta.
A hankali sai zuciyarta da kuma tunaninta suka fara komawa baya suna mata tunin wasu abubuwa da suka faru shekarun baya da suka shude.
WANNE QULLI NE ZARGE QARQASHIN WANNAN IYALI DAKE DADADADDEN TARIHI?,SANIN KOMAI DANGANE DA TARIHIN WANNAN AHALI SHINE TAMKAR MADUBI HASKE KUMA FITILA TA LABARIN GABA DAYA
WHO DIED? WHO LIVES?
MUHAMMAT MAYAK’I
Dattijon arziqi shine sunan da jama’a da yawa ke kiransa dashi cikin ainihin mahaifarsa dake qasar nijer garin AGADEZ. Garin da ya zama tushe kuma makafar buzayen dake qasar nijer din.
Babban family garesu wanda yayi tambari sannan yayi suna ta fannin ilimi siyasa da kuma arziqin kansa. NADEEYA na daya daga cikin mutanen da suka sake sanya sunan family din MAYAK’I yayi shuhura. Qasaitacciyar ‘yar boko ‘yar kasuwa,wadda Allah ya huwacewa baiwar kwanya basira da iya sarrafa rayuwa. Gefe guda kuma tana daya daga cikin matan da koda cikin buzaye kyawunsu na dabanne. Wani irin kyau da akayi ittifaqin har xuwa yanzu shike bibiyar jininta,’ya’ya da kuma jikokinta. NADEEYA din ta fita daban,saidai a yanzun za’a iya cewa HAMDIYYA ABDU ME KANO wato AMA ita ke biye da sawayen NADEEYA da dukka tarin wadannan abubuwan da nadeeya din ta mallaka tamkar dama can ama ta fito daga tsatson nadeeya dinne. Saidai Sam,ita kanta ama batasan nadeeya da idanu ba wadda su aba ke kira da granny saboda ita din kaka ce a wajensu.
Ko cikin mata nadeeya ta dabance,wanann ya sanya ake tunanin ya zame mata kambun data riqa wanda ta zauna gaban Bobbi wato kakansu aba ita daya tal!,har zuwa lokacin da bobbi din ya rasu ya barta. Ita daya taci gaba da kula da ‘ya’yanta cinsu shansu karatunsu har zuwa tarbiyyarsu. Allah ya albarkaceta da yara maza ne gaba daya su biyu,tayi mata sau biyu suna rasuwa,duk yadda takeson ta ganta da ‘yar budurwa haka ta haqura. Allah ya raya mata yaranta rayuwa me kyau. ABDALLAH shine babban d’anta da ya zame mata gishiqi kuma madogara,wanda ta dora bisa dukkan wasu hanyoyi nata saboda halin rayuwa. Ya kama kuwa fiye da yadda ma takeso,wannan ya kwantar mata da hankali,saidai duk da haka bata nutsu ba har sai data tabbatar ta aurar dashi shi da me binsa wato ABDURRA’UF.
ABDALLAH ya auri bibi nana halimatou asalin bafulatana kuma buzuwa ‘yar asalin garin AGADEZ. Kafin ya samu daukar halimatou bibi yasha fama a lokacin saboda wani irin farinjini Allah yayi mata,hakan kuma itama baya rasa nasaba da zallar kyau da Allah ya huwace mata,uwa uba tana da wata irin nutsuwa kamun kai da cikakkiyar tarbiyyar da takai duk yammatan unguwarsu idan an tashi kwatance da ita akeyi musu.
Gida guda nadeeya ta gina musu ita da yaranta,saboda tana da sha’awar su rayu tare. Wani irin gini tayi musu mahadi ka ture,ginin da saidai gidan sarakuna da manya manyan attajirai irinta.
Rayuwarsu na tafiya kaman yadda nadeeya ke buri,tsufa yana dada kamata,amma kulawar da take samu ya sanya take da cikakkiyar lafiyar da ciwo dai saidai irin wanda me dattijan da shekaru suka soma musu rubdugu basa rabuwa dasu.
A hankali bibi ta soma hayyafa,saidai faccalarta aseeya har zuwa lokacin shuru. Ba wanda ya daga mata hankali ko ya daga nasa hankalin,saboda dukkansu masu aiki da ilimi ne.
Dukkan me rai mamaci ne,sanda bibi keda yaranta maza har guda shida a lokacin ajali ya saukarwa granny nadeeya,lafiya lau akayi sallama da ita da dare ta tafi ta kwanta aka wayi gari babu ita. Sunyi kuka,sun kuma shiga tashin hankali sosai,saboda tsanani sabo da shaquwa da kulawar da suke samu daga yaran nata har jikokinta. Tayi masifar dasa musu wata irin qaunar juna a tsakaninsu,bawa juna kulawa da damuwa da damuwar juna, dabi’ar data bi jininsu qwarai da gaske,ta kuma zarce cikin jikin jikokinta har zuwa sanda suka zama cikakkun samari.
MOHMOUD da HAMIDOU sune yaran da bibi ta haifa da tazarar shekara hudu a tsakaninsu,batayi haihuwa ta uku ba kuma sai data shekara biyar ra haihuwar HAMIDOU(ABA) sannan ta haifi MUHAMMAT,sai oumar bashar sannan issoufou autah.
Babban tashin hankalin da suka fuskanta bayan rasa nadeeya shine na rasuwar mahaifinsu alhaji ABDALLAH wanda gaba daya sunansa yafi fice da sunan kakansu na ainihi wato MAYAK’I. Rasuwar da tayi mugun girgiza su,ta kuma daga musu hankali,don shi dinma kamar dai nadeeyan,babu wani ciwo,face dai tunanin da suke rasuwar mahaifiyar tasa ya maqale a rai har ta zame masa ajali. Hakanan cikin wani irin ciwo da rashin rabo sukaci gaba da rayuwa,cikin rashin jin dadi da kuma walagigi saboda basu saba rayuwa haka ba su kadai,don kuwa a sannan baaba ABDURRA’UF yayi nisa da agadez,bama agadez ba gaba daya nijer,tun bayan rasuwa granny da aka bashi gadonsa ya lula duniya fatauci.
Tun bayan tafiyarsa sai matsalolin rayuwa suka dinga taso musu,wadansu mutane sabbin fuska da basusansu ba,kowa yazo zaice yana bin nadeeya ko abdallah abu kaza,sai sunyi duba da wani abu me qwari cikin dukiyarsa suce yayi jinginarsa a garesu. Babu wanda bibi ta tsaya ja’inja dashi,ta barsu kawai,a sannan mohmoud yaso ya taka birki duk da kwata kwata shekarunsa a sannan basu goma sha biyar ba amma bibi ta hanashi
“Zukatan mutane a yanzu sun qeqashe da son abun duniya,komai na duniya a nan aka sameshi kuma a nan za’a barshi,yau ina wanda ya tara dukiyarma?,ka barsu nafi buqatar taka rayuwar akan abinda aka tara muku,watan watarana sai kaga Allah ya albarkaceku da abinda yafi abinda kuka rasa” qananun shekaru da kuma zantukan bibi ya sanya hakanan suka zuba ido,basu qyalesu ba saida suka tabbatar sun rabasu da manyan kadarorin da mayak’i ya mallaka.
Shekarar da mohmoud ke aji na biyu na university,hamidou (aba) yake ajin qarshe na secondry school rayuwa ta tsananta a garesu,gidan da suke ciki ma ya soma niyyar gagararsu zama a ciki. MOHMOUD wani irin halitta ta daban Allah yayi masa,bibi tasha daga hannu ta godewa Allah da ya bata kyautar mohmoud a matsayin d’a. Yana da kyakkyawar zuciyar da zai iya yin kuka saboda kawai wani yayi dariya. Yana da kyakkyawar zuciyar da zai iya hanawa kansa saboda wani ya samu,yana da kyakkyawar zuciyar da zai iya wanzuwa cikin radadi rudani da firgici muddin wani zai wanzu cikin walwala nutsuwa da kuma sukuni. Wanna dabi’a tasa bawai iya cikin gida ba har zuwa ga mutanen waje.
Ranar da abun yaci tura ranar da ya kammala jarabawarsa ne daga aji biyu zai shiga aji uku,sakamakon jarabawar hamidou kuma ya fito,an gama komai na cuku cukun tafiyarsa jamia,amma kudin da ake da buqata don yiwuwar hakan basu babu dalilinsu.
Idanunsu jajur yayi zaune gaban bibi yana gaya mata ya ajjiye karatunsa,ya yanke shawarar bidar kudi kota halin qaqa kota kuma wacce hanya muddin wannan hanyar halastacciya ce don ya kula da ita ya kuma kula da rayuwar qannensa
“Amma mohmoud ta yaya?,karatun naka dake sake nisa ta yaya zaka ajeshi?” Kai ya girgiza
“Sam sam karatuna a yanzu bashi da amfani,koda na yishi bazanyi farinciki ba mahaifiyata da qannena da basu da kamata suna cikin matsi da buqatar rayuwa” daga bibi har hamidou tsit sukayi suna duban mohmoud,ya fadi maganar ne har tsakiyar rai da zuciyarsa. Daga kuma randa ya furta wannan batu ya fara aiwatar da abinda ya tsara din kamar yadda yace.
Tinja tinja aka dinga yi tsakaninsa da hamidou,yace shi kuma sam bai yarda ba,bazai zama silar rujewar farinciki da kuma burikansa da shi yafi kowa saninsu ba. MOHMOUD bashi da wani babban buri a duniya da ya wuce ya zama cikakken likita,ya shaidawa bibi shine zai tallafi karatun yayan nasa,idan yayan nasa ya gama shi yayi nasa.
Wani kallo sheqeqe ya watsawa hamidou,har yanxu wannan kyakkyawar soyayyar da qaunar da granny nadeeya ta dasa musu yana biye da jinin jikinsu
“Saboda gani babban banza ko?, bakaji mr bahausa suka ce ba?, babban wa magajin uba ko?,to gwara ka soma shirin tafiyarka makaranta,don ko bakaje din ba dama karatuna tangal tangal yakeyi ai, karatun lafiya sai dan wane da wane kai kafi kowa sanin haka,ni ba babbabn kwabo bane ra zan zauna qanina ne zai tallafi buqatun qannena dana mahaifiyata ba,indai nayi hakan meye amfani na?,meye amfanin girman da Allah ya bani?”.
Tun daga lokacin da ya ajjiye karatunsa ya shiga neman kudi idanu rufe saidai bisa tsaftatacciyar hanya,baya raina abinda zaya kawo masa kudi komai qanqantarsa koda kuwa kwasar kashi ce. MOHMOUD dan gayu dan gata sai gashi tashi daya rayuwa na tamaula dashi tana sauya masa kamanni da tsarin rayuwa. Yasha dawowa gida ya kasa bacci saboda ciwon jiki ciwon kai ko ciwon qafafu,amma baya bari kowa ya sani. Saidai kuma wannan dashashiyar qaunar tana nan tana kewayawa,duk wani motsin MAHMOUD din bisa idanu da kiyayewar HAMIDOU ne, hamidou din yasha boyewa yayi kuka saboda ganin yadda yayan nasu ke bautar da kansa saboda su,iya yadda yake tunanin yaa mohmoud yana sonsu sai a yanzu ya tabbatar abun ya zarce haka,ya kuma shallake hankali da tunaninsa. MOHMOUD ne faskare, MAHMOUD ne tura ruwa, MAHMOUD ne dako, MAHMOUD ne share share goge goge da wanke wanke a gidajen saida abinci duk don kada karatun hamidou ya samu tangarda,kada karatun su oumar ya tsaya,kada bibi ta buqaci wani abun ta rasa,ya gwammace shi yayi kuka muddin su zasuyi dariya. Ranar da ya gaza jurewa ganin dan uwan nasa ahaka cikin wani darene da MAHMOUD din ya kasa bacci saboda radadi da hannunsa ke masa saboda yawan itacen daya faskara duk don ya qarasa hada kudin registration din hamidou.
Yana ganin hamidou din ya motsa yayi saurin boye hannuwansa,saidai kuma tuni shima ya kama hannuwan yana kalla. Wasu hawaye suka zarto daga idanunsa yana dubansa
“Hamma….wannan abun da kakeyi a kanmu yayi yawa,ka sassauta gangar jiki da zuciyarka don Allah hamma” hamidou ya fada yana hawaye. Jawoshi kawai mohmoud yayi yana bubbuga bayansa
“Inajinku ne tamkar ‘ya’yan da suka fita a ciki na,zuciyata da ruhina ba zasu taba samun nutsuwa ba muddin dayanku na cikin buqata” sun jima a daren hamidou yana gasa masa hannunsa,tun kuma daga ranar yasa ya masa alqawarin daina boye masa wasu abubuwan,sannan wasu lokutan tare suke fita ayyukan,amma yanayin karatu ba kasafai yake barin hamidou din binsa ba. Shima kuma MAHMOUD din yafison hakan,yace yafison yayi zamansa ya maida hankalinsa akan karatunsa shi shine farincikinsa…….
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 04
HAMDIYYA ABDU ME KANO
Yarinyar da tafi kowa kyau cikin school din,ajjiye kyau a gefe,idan ana batun gata za’a iya cewa kaf makarantar babu diyan da ya kaita gata wala mace ko namiji.
Ita din diya ce ga attajiri alhaji abdullahi me kano,mashahurin dan kasuwa wanda inda arziqi yana yawa za’a iya cewa nashin har yayi yawa. Arziqi da aka nemeshi da zuciya da kuma qwanji,aka tara shi cikin albarka iyaye data al’umma. Yaranshi uku kacal a duniya,tajuddeen da ake kira da taj,sai mebi masa abdulhakeem sai kuma ‘yar daya daya ‘yar gatansu kuma ‘yar gaban goshin kowa wato hamdiyya(ama). An haifi hamdiyya ne a lokacin da kowa ya fidda rai daga sake samun haihuwar mahaifiyarta hajiya aisha a duniya,bayan wasu shekaru harsu abdulhakeem sun fara yin hankali,don a qalla a cikinsu babu wanda ya bata qasa da shekara goma. Tazo a dai dai sanda suke da kwadayin qananun yara a gidan,kuma tazo a jinsin diya macen da basu da ita,wannan ya sanya gata yayi mata rubdugu tako ina,kowa kawo nashi gudunmawar gatan yakeyi. Idan akace gata ana nufin gata me sunan gata,gatan da ya sanya take cike da haushin yadda rayuwar sultana take,domin kuwa idan za’a dora mizanin gatan da sultana ke samu da wanda ita ta samu a zamanin quruciya zata iya cewa sultana din bata samu kaso daya cikin goman nata gatan ba,saidai natan bai hanata samun cikakkiyar tarbiyya da kulawa ba. Sam sam alhaj abdullahi da aishatu matarsa basa cikin jerin sahun mutanen da suka aza dukiya a gaban tarbiyya yaransu. Sau da dama yanayin tarbiyya yaran alhaji abdullahi na bawa daruruwan mutane mamaki. A yadda mahaifinsu keda kudi ruwa ruwa kamar su kasheshi,ko kadan ba zaka taba tsammatar samun tarbiyya haka daga yaransa ba,sakamakon yadda ya zama kamar wani tambari ko al’ada na yaran da iyayensu ke da hali,sukan tashi a sangarce,babu ganin girman babba bare akai ga sanin haqqin qarami,gaisuwa ma kam ba kowanne ke tashi da iyata ba,wanda wannan babban kuskure ne ga rayuwa,domin da ‘ya’ya da dukiya dukka amana ce kuma jarrabawa ce,idan ka jagorancesu ta hanya me kyau kaci moriyarsu cikin kwanciyar hankali da farinciki,idan ka jasu kuma ta akasin hakan lallai bone da nadama yana nan tafe.
Hajiya aishatu mahaifiyar ama itace haifaffiyar qasar NIJER, CIKAKKIYAR buzuwa gaba da baya wadda har rayuwa tayi mata zurfi cikin nijeria bakinta baya fidda hausa tar kamar yadda ya kamata.
Sun rayu kuma tashi da tsananin zumunci,daga dangin mahaifi har na mahaifiya babu wanda suka bari a baya wajen sada zumuncinsu,wannan ya sanya alaqa me qarfi tsakaninsu da dangin mahaifiyarsu dake nijer. A duk sanda suka samu hutu suna ware lokaci sosai da zasuje ga dangin mahaifiyarsun suyi masu kwanaki su juyo,wannan ya sanya nijer taso janye hamdiyya banda tsananin son da suke mata da tuni zamanta a Nigeria ya zama labari,saidai duk da hakan bayan ta kammala secondry school kakarta ta dauketa da zummar hutu kawai zatayi ta dawo,sai gashi zama ya miqa,duk da yadda abbanta dama su abdulhakeem ke jelen ta dawo gida
“Yo ku meye naku ne bayan kowannenku yana nashi gidan da iyalinsa?,ku jiyemin yara da sanabe?” Hajja kakarsu ta fadi tana kama haba
“Gidan ne ba kowa fa,daga maama sai masu aiki” tajuddeen ya fada
“Sai kuma kayita yi,amma tabbas jikina ya bani nijer saita janye hamdiyya” ta fadi saboda yadda taga tana sha’awar qasar sosai da son zuwa tare da son zama a cikinta.
Kai tsaye qanin mahaifiyarta ya soma mata cuku cuku sanda aka fara diban dalibai a matakin karatu na gaba da secondry. A tsarin jami’ar hamdiyya bata da wani aibu ko nakasu da zaya hanata samun gurbi. Results dinta sunyi kyau har abun ya dinga basu mamaki,saidai kuma ba abun mamaki bane,saboda baiwar wata budaddiyar kwanya Allah ya bawa ita hamdiyya din,abun kuma sai ya hadu da nacin son karatu da take dashi.
Sanda ta shiga makarantar hamidou(aba) yana aji uku,kuma shine president na makarantar gaba daya. Ranar data fara zuwa ranar ta fara ganin aba din, saboda a ranar sun gudanar da zanga zangar lumana cikin makarantar. Tana zaune daga qasan bishiya tana jiran driver ya iso ya dauketa,tanata zumbura baki irin na yaran da gata ya yiwa yawa,tana jin yadda zafin rana ya bude a sararin makarantar ya hadu da rairayin yashi yake bada wani hucin zafi har saman fatarta,daidai sanda dandazon matasan makarantar suke yowa ta area din da take.
Tsaki taja me qarfi tana qorafi cikin ranta na yadda ko zafin ranar sukam basuji?. Tana zaune har suka qaraso inda take suna wucewa da ifce ifcensu wanda yake cikin tsari ne ba hauka bare sauka daga tsari.
Da idanu take binsu kawai bakinta a tabe daya bayan daya,tanason gano waye shugaban wannan wahalar?,sukam me suka rasa da zasu damu kansu da surutai haka da rally cikin makaranta?. Caraf idanunta ya sauka saman fuskar kyakkyawan matashin buzun. Sanye yake da wasu jajayen kaya da baqar p cap wadda duk da ta dan rufe fuskarsa kadan amma hakan bai hanata hango gumi da yadan jiqa goshinsa ba,ya kuma bada damshi saman kyakkyawar fuskarsa dake da wani irin sassanyan kyau me matuqar jan hankali.
Kaf yawun bakinta ya katse,ta qifta idanunta ta sake budesu duka lokaci guda tana hadiye busashen miyau din da yayi saura a bakinta. Tunda take zata iya cewa idanuwanta basu taba tozali da namiji me kyan aba ba.
Bata cika buri cikin rayuwa ba,bata da wulaqanci sai son jama’a da take dashi,bata da daukan rayuwa da zafi saboda ta fito daga gidan wadata,amma kuma tana da wani buri qwaya daya da kaf gidansu hatta da abbanta da wasu makusantanta na kurkusa sunsan dashi,wato tana son KYAKKYAWAN NAMIJI. Ba wai abu bane data tsireshi bayan ta girma ba,ko kuma bayan ta fahimci ita dinma me kyau ce ajin farko, a’ah tun tana qanqanuwarta take da wannan dabi’ar. Mama mahaifiyarta bata zafafa mata ba tun daga quruciyar,saidai ta zafafa wajen addu’ar idan ta isa munzali qaddarar aure ta zowa diyartata ubangiji ya hadata da nagartaccen miji salihi kuma managarci. Tun su abdulhakeem suna tsokanarta har suka fahimci da gasken gaske a jininta ne kuma raayinta ne hakan,sai suka daina tsokanar suma sai lokaci bayan lokaci.
Akwai tarin maza da suka amsa sunansu,masu kyau irin kyan nan abun kwatance da suke maqurar qaunarta da neman soyayyarta,to amma sai Allah ya sanya mata wani irin hali na shariya da miskilanci. Duk son jama’arta da haba haba dinta miskilar kanta ce idan taso.
Bada umarnin da aba yayi wajen dakatawa aje a bada faralin sallah ya sake fusgar hankalinta,tana nan a zaune taron ya watse,ya nufi hanyar masallacin makarantar bangaren maza yana zare pcap din kansa shi da ‘yan tawagarsa suna tattaunawa,cire hular kuma da ya sake bayyanar mata da asalin kyansa.
Tun daga ranar bata sake ganinsa ba,hakanan zuciyarta bata huta da tunanin waccan ranar ba. Bata kuma sake ganin nasa ba sai bayan watanni shida,karatunta ya soma yin nisa,ana shirye shiryen fara exams da tafiya hutu. A sannan ne dalibai suka qirqiri wasu programs da sukan gabatar a lokuta irin wadannan,ciki harda zaben sarauniyar kyau ta makarantar.
A lokacin sai kawai gani tayi sunanta ya fita cikin list din wadanda zasu tsaya a matsayin. Ranta ya baci hankalinta kuma ya tashi. Tana da qawaye tunda ita din macace me kirki,bata raba dayan biyun a cikinsunne wata ta bada sunanta,kuma tunaninta ya tafi kan mutum daya data tabbatar bazata wuce ita bace wato ummuhani mammadou. Koda ta tuhumeta din kuwa ita dince. Fada ta balbaleta dashi akan ba zata shiga ba,tace kuma tun wuri su zame sunanta don ba abinda tazo yi ba kenan.
Lokacin aba na zaune cikin ‘yan kwamitin tsare tsare ummahani ta shaidawa hafeez wanda shi ya qirqiri abun cewa hamdiyya na buqatar a zame sunanta,ta kuma baiwa hafeez haquri,wanda koda bayan ummahani ta wuce bai fasa qorafi ba
“Ita daya ce zata sanya makarantarmu taci wannan competition din,yanzun wace zata maye mana gurbinta?”
“A soke wannan cikin tsare tsarenmu hafeez, banason irin wadannan abubuwan” shine kawai abinda aba yace.
Bai taba ganinta ko lura da wanzuwarta ba sai ranar da aka fara programs din. Sai kuma a ranar program din da aba yace a soke yaji basu soke din ba,don a wajen aka fara neman ‘yammatan da suka shiga suzo su fara rehearsal.
Ko motsi hamdiyya batayiba sanda aka kira sunanta saboda tasan tuni ta bada sanarwar fita daga lamarin. Aka dinga maimaita kiran sunanta amma ko motsi,abinda ya sanya MC pointing dinta don shi ya hangota,take kuwa idanu sukayi caaa a kanta. Adadin idanuwan ya sanya kanta sarawa,sai kawai ta miqe tsam ta dinga ratsawa ta cikin jama’a har ta fice daga hall din.
Haka kawai aba yaji ranshi yayi matuqar baci,bai wata wata ba ya karbi mic daga hannun mc din ya fara bada sanarwa dakatar da shirin. Sanarwar data hargitsa hall din qananun maganganu suka dinga tashi,shidai a matsayinsa na shugaba ya riga ya zartar da hukunci,ya tabbatar kuma dukka mataimakansa ba wanda zaija da hakan saboda zuwan halayensu kusan iri daya,sai kawai ya saka kai shima yana barin hall din.
Baisan tana ta wajejen ba sai daya isa ya tsaya yana furzar da iska sai yaji sautin sheshsheqar kuka kuma ana waya
“Kice musu su qaraso su daukeni gida zan koma” idanu ya zuba mata cikin mamakin yadda qatuwar budurwa irin haka ke kuka shabe shabe da hawaye,jajayen labbanta sun sakeyin ja haka bakinta. Taku biyu tayi Don gyara tsaiwarta santsin wajen ya kwasheta zata fadi. Da hanzari yakai mata taimako Allah ya taqaita kafin ya isa gareta ta samu ta dafa wata qaramar bishiya ta tsaya
“Ki ding kula mana” ya fada cikin nuna damuwa. Kai ta daga da sauri,idanunsu suka gauraya waje guda,wani irin abu me qarfi ya sauka zuciya da gangar jikin kowannensu,sai kowa cikinsu yayi hanzarin janyewa da baya,yayin da ciwon kan hamdiyya ya qaru har sai data saka hannu tadan riqe kan
“Baki da lafiya?” Ya tambayeta yana qoqarin kallon qwayar idanunta. Idonta ta lumshe tana jin yadda zuciyarta ke wani irin bugu da bata taba yi ba ta gyada masa kai
“Saiki tafi gida ko ki wuce hostel ki nema magani Kisha” ya fadi yana janyewa baya saboda shi din ba gwanin kula mata bane.
Ta qasa qasa take kallonsa,qafafunsa sake cikin wasu Black sneakers na motsawa da alama wajen zaya bari
“Ka taimakeni ka miqani gida,bazan iya tuqi ba,bani da nisa daga nan” dukka ta bashi maganar lokaci daya. Dan jim yayi yana kallonta duk da baya iya ganin zahirin fuskarta. Kamar zai musanta sai kuma ya tuna da maganar da Bibi ke yawan gaya masu
“Su mata ababen tausayi ne,a duk sanda suke cikin taimako ku taimaka musu gwargwadon iyawarku” wannan maganar ta sanya ya koma ya amshi key din a hannunta yana satar kallonta,haka kawai zuciyarsa ke bugawa a kanta tun ganin farko da yayi mata dazun. Ya zagaya ya bude mata ta shiga sannan ya rufe ya dawo ya shiga shima ya tayar da motar yana godewa Allah da ya sanya ya koyi mota da yau baisan yadda zaiyi ba.
Yadda yake tafiya a hankali da motar,da alama kuma yana yin hakanne dukka don ciwon kan nata sai ya sake narkar mata da zuciya a kansa,sai take ganin yaa tajuddeen da yaa abdulhakeem tattare dashi,haka suke mata irin wannan riritawar. Zuciyarta nata mata saqe saqe akansa,yayin da shi kuma yayi nisa wajen satar kallonta ta cikin madubin gaban motar yana tsarkake ubangiji da irin kyawun halittar da ya bata.
Ita ta dinga kwatanta masa hanya har suka iso gidan,a LOKACIN sai da jininsa yadan daskare na wucin gadi,tsoro kuma ya kamashi na ganin yarinyar da ya rako
“Yanzun idan tayi maka wani qazafin fa?” Abinda ya bashi fargaba kenan,amma da yake namijin duniya ne sai ya daure ya cusa hancin motar har zuwa farfajiyar gidan.
Sanda dukkansu suka fito a motar sai kowa ya rasa bakin magana,ita tana tauna abinda zatace ne kada ta zubda ajinta da kimarta na mace,shi kuma yana dari d’arin ya kawo kansa gidan dafa kansa.
Muryar hajja ta katsesu ta qaraso tare da uncle din hamdiyya. Cikin nuna matuqar kulawa take dubanta kamar tana neman gurin da aka gutsireta tana tambayarta
“Ya akayi kika iya dawowa da kanki?,ke da nace ki jira su soja sun tafi dauko mato daga airport suna kusa daku saisu daukoki?” Hamidou ta nunawa hajja tana mata bayanin shine ya taimaketa. Abinda ya daure masa kai harda qarawa abun gishiri da armashi.
Kaman hajja ta goyashi haka ta dinga zuba masa godiya tamkar wanda ya qwato mata jika daga wajen kidnappers. Hanashi tafiya hajja tayi,cikin lokaci kadan sai gashi ta sanyashi ta dole ya sake cikin gidan. Cikin mintuna kadan yaga kamanceceniyar halaye tsakaninta da granny nadeeya dinsu da har yau basu manta da ita ba. Ya kusa awa daya tana jansa da hira,sannan ta cika masa gaba da kayan ciye ciye. Koda ya tashi tafiya amana me nauyi ta aza masa,wato amanar kula da jikarta
“Ka taimaka.ka karbi wannan aikin,duk da nasan na aza maka nauyi,don Allah,saboda kowacce makaranta akwai bata gari na sani,to amma zasu kiyaye idan sunsan akwai wani namiji a tare da ita,nayi nayi a sama mata masu tsaron lafiya koda mutum biyu ne amma ta qiya,ita wai sam batason irin wannan rayuwar” dan satar kallonta aba yayi,daga yanayinta kawai da yadda yazo ya samu family dinta yasan lallai tana da sauqin kai da rashin daukar rayuwa da zafi,a arziqin da Allah yayi musu yayi imanin inda watace ma sam tabar rayuwa a Nigeria.
Tsohuwar ta masa kwarjini da yawa dole ya karbi amanar hamdiyya ba don ya shirya ba. Wanda hakan ya fara kawo alaqa tsakaninsu me qarfi,ta dauke tamkar yayanta,shima kuma kaman qanwarsa,wani lokaci ma tare suke tafiya makaranta cikin motarta,donma yana goggocewa kasancewarsa mutum da ya iya kamun kansa yasan kuma kimar martaba da darajarsa. Duk da haka komai nata saita tsomashi a ciki,idan yaqi ma takan hadashi da tsohuwar dole saboda girmamawa yayi din.
Shi da ita dukkansu soyayya tayi musu mugun kamun da basu zata ba,ga hamdiyya dai tasan tabbas ta fada dumu dumu cikin soyyayar hamidou,amma kuma ba zata taba yin abinda zai watsa mutunci da darajarta ta diya mace ba. Abinda bata sani ha hamidou ya fita shiga garari,domin kuwa kusan har walwalarsa abun yaso.tabawa,daga bibi har hamma mohmoud ba wanda bai Kula ba,tambayar duniya ya kasa basu amsa,saboda shi kansa yasan bai daukowa kansa da su turba me bullewa ba,su da suke ririta rayuwarsu ta yaya zai dauko wannan babban aiki?.
A yanzun yana tsaka da karatunsa kuma nauyinsa yana wuyan wani mutum ne wato mohmoud,mohmoud din da ya kashe tasa rayuwar saboda ya raya tasa rayuwar?,ta yaya zai iya duban qwayar idanunsu yace ya fada soyayya?.
*KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 05
“………….ya fada soyayya?,yana nufin kenan aure yake da buqatar yi?,bama fadawa soyayyar ba,wadda ya fada soyayyar da ita, yarinyar dake da gatan da ya kerewa nasa,suke da dukiya da tarin gatan da ya yiwa hankali nisan tazara,kai koda ma ace ya kammala karatunsa ya kama aiki ina yaga kudin auren hamdiyya abdu me kano?,ko yana da kudin aurenta dinmma sakayyar da zai yiwa bibi da mohmoud dake tsaye a kansa ba dare ba rana?,ya tattara ‘yan kudinsa yayi aure ba tare da sun mori komai daga gareshi na wahalar da suka sha dashi ba?. Kansa ya girgiza yana bawa kansa amsa da A’AH,ya zama dole ya sake nisanta kansa da zuciyarsa daga soyayyar hamdiyya,hatta da mohmoud sai yanzun yaga an fara tada zancan aurenshi,idan bai manta ba wancan satin yaga ya fara shigo da akwati guda uku bibi na mata wajen ajiya,ta yaya shi da yaie sanya ran zai zamesu musu sanyin idaniya ya buge da wannan zancan?. Dama bai bari ko kadan zancan hamdiyya ya fasu cikin gidansu ba saboda gudun tashin hankalin bibi da kullum tsaronta akansu ne,sai kawai ya yanke shawarar fara janye jiki daga gareta da kuma dukkan al’amuranta.
Hakan bai haifar da komai ba saima sake dagula al’amarin da yayi,ta zube dukkan wautar dan fari da shagwabarta,kwatsam sai kawai gashi ta dauko mahaifinta tun daga Nigeria yayo tattaki ya iskeshi har cikin makaranta wai yazo sasantashi da hamdiyya,tace batasan laifin data yiwa yayanta hamidou ba yake gudunta. A ranar hankalinsa yayi matuqar tashi,ganin babban mutum me girman daraja wai yazo gareshi ban haquri?.
Kame kame ya dinga yiwa abban don baisan ma me zaice masa ba. Daga qarshe kawao abban ya saki murmushi yana dubansu
“Inaga gwara kawai na yanke muku wannan wahalar da kukeyi akan juna,kai yayan hamdiyya,indai ka aminta kanason hamdiyya ka shaidamin zan baka aurenta,ku sasanta kanku bari na baku waje” abinda abba ya fada kenan ya fita daga wajen cin abincin daya kama musu table daya.
Kamar zata hadiye zuciyarta haka ama taji sanda taji furucin bakin mahaifinta,tabbas inda ace ita daya ce a wajen ihu zatayi tayi tsalle tayi shewa,amma.yanzun duk yadda albishiri din yakai ga faranta mata dole ta kame kanta ta kuma zuba masa idanu tana jiran jin ta bakinsa. Kau dakai tayi sanda yayi nufin kallonta,a yanzun yana jin bazai iya boye mata komai ba
“Ina tsananin qaunarki hamdiyya bazan iya boye miki ba,amma kuma bani da halin aurenki saboda a yanxu nidin ba kowa bane,kuma bani da komai ban kuma bawa kowa ajiya ba,idan nace zan aureki hamdiyya na cutar dake,bani da arziqin riqeki,ki bari kiyi aurenki na gata,ki auri dan gata irinki da zai iya baki irin rayuwar data dace dake…”
“Ba wanda yayimin cikin maza babu kuma wanda nakeso saikai, hamidou xan aura ba alatun duniya ba,dukka maganganunka a yanxun ba hujja bane,saidai idan kanaso ka fake ne,ni hamdiyya ban maka ba” ta fadi tasirin sonsa na yawo cikin idanunta da wani irin kaifi.
Duk da ba’a mode da zaiyi dariya suke ba amma sai daya murmusa,bayajin tana masa rabin son da Allah ya jarabceshi dashi nata
“Baya ga bibi da ‘yan uwana ban taba jin soyayyar wata halitta a zuciyata ba haka…..”
“Indai hakane ka sanya a ranka ni hamdiyya matarka ce,ban kuma fi qarfinka ba” ta tari numfashinsa kai tsaye.
A nan gurin ta lalata masa dukkan wani tunani nasa da zazzafar soyayyarta ta hanyar kalaman bakinta,suka rabu suna kewar juna ainun saboda a yau din dukka wani qulli ya kwance soyayya kuma tayi ambaliya ta bayyana kanta.
Wajen tara na dare yana rungume da littafi yanason yayi karatu amma ya kasa saboda tunaninta,wayar hannu sai me wadata,su dinma ada akwaita cikin gidan,amma yanzun da rayuwar ke neman fin qarfinsu dole suka sakata a kasuwa suka saida.
Yana kwance daga daki yana jiyo hirar bibi da mohmoud,ya dawo daga aiki futu futu da tarin gajiya bibi ta zaunar dashi tace sai ya fara cin abinci kafin yayi wanka. A hankali yaji suna sako batun aurensa da bintou,da yadda za’a yi asiri ya rufu ayi komai a gama,don ma itama bintou din ba yar gidan wani bace,asalima bafulatanar katsina ce,yanayin aiki ya kawosu nan din,saidai kuma suna da tarin rufin asiri daidai gwargwadon yadda dan adam zai iya rayuwa cikin walwala. Yadda yaji suna maganar ya sake sanyayar masa da jiki,sai yaji batun hamdiyya tamkar ya ajeshi a gefe don baiga ta inda zai yiwu ba.
Washegari jinkirin isowarta makaranta kadai akan lokaci ya hautsinashi,ya gaza shiga aji ya zauna har sai da driver dinta ya ajeta. Ta fito tana masa hararar wasa da fararen idanunta
“Kada kacemin komai,ina shakka akan son da kace kana yimin,tunda har na qara awa daya kusan da rabi amma ka gaza zuwa ka taho dani har sai da driver ya taho dani” murmushi kawai yayi yana jin sassauci cikin qirjinsa tunda ta iso lafiya.
A ranar kafin su rabu ta damqa masa waya me kyau a hannunsa
“Mu dinga communicating,dare yanamin tsaho kafin wayewar gari nazo na ganka” amsa din kawai yayi yana juyata a hannunsa,bayason zaqewa ko zura jiki da yawa,bayason kuma su sake nisa shi da ita abun yazo baiyiwu ba ya zame musu ciwo shi da ita. Baice bazai karba ba bai kuma ce ya karba din ba,yabar wayar a hannunsa dai ya kuma shiga gidansu da ita.
Sam ya manta tana jikinsa har suka gama hira da bibi yaci abincinsa,yana shirin shiga daki ya watsa ruwa kira ya shigo,shi da bibi din duk sukayi sak sai ya ciro wayar yana dubawa. Alarm ne, kasheshi yayi ya matsa gaba ya ajjiye wayar gaban bibi yau yana yankewa a ransa ya shaidawa bibi komai,tunda cikin maganganun da sukayi a yau da hamdiyya ta shaida masa abbanta ya bawa aba din damar fitowa neman aurenta saboda duniya ta shaida shima ya huta da zirya da neman irinta da ake faman zuwan masa.
Yana fara gayama bibi komai sai ga mohmoud shima ya shigo,duk da lokacin shigowarsa baiyi ba,hannunsa biyu dauke da.ledoji niqi niqi yana fadin
“Bibi yau nayi babban samu,nace bazan iya jira lokacin tashi yayi ba banzo na shaida miki addu’arki ta daren jiya ta karbu ba,bibi yau kaji kawai zamuci a gidannan” yanayin da ya gansu ya sassauta karsashinsa,sai bibi ta nuna masa gefanta
“Zauna nan” ba musu ya aje ledojin ya kuma zauna din,aba kuma ya dora da bayaninsa.
Bai boye musu komai ba,komai ya bayyana musu,falon yayi shuru kowa yana juya abun cikin ransa. Tsahon wasu mintuna sannan bibi tace
“Kai yanzun kana ganin hamdiyya kininka ce?” Ta jefa masa tambayar kai tsaye wadda ya kasa amsa mata
“Banason na sake jin wannan zancan,hamdiyya ba tsararka bace,koda ka dage kan zaka aureta ba lallai ka samu abinda kakeso daga matarka ba,cikin abinda akeson miji yafi matarsa akwai dukiya wadda kusan ita ke riqe da auren,kai kuma baka da ita,uwa uba ma yanzun haka dan uwanka ake maganar ya samu ya fara auren,kada na sake jin wannan batun”
“In sha Allah” ya amsa mata cikin matuqar girmamawa,har ransa kuma yakejin ya gamsu da hakan zai kuma yi qoqarin bi iyakacin qarfinsa.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 06
Shi da hamdiyya dukka sun dauki abun da wasa,bayan ya shaida mata zai haqura din saboda rashin goyon bayan mahaifiyarsa da bai samu ba,ita dinma zuciyarta tadan tabu,kuka ta amince zata dafa masa baya akan hakan,amma sai su duka zukatansu suja gaza jurewar. Qarewa suka dinga yi suna rama shi da ita harda qananun lalure lalure,at last dai abban hamdiyya ya sake shiha maganar,yayi tattaki da kansa ya iske bibi har gida,ya kuma bata tabbacin amincewarsa shi da hamdiyya din,sannan kuma ya qara mata da albishir din cewa baya buqatar komai daga hannun hamidou illa sadaki. Abban hamdiyya ya barsu da tarin kyautatawa da alkhairinsa wanda baya boyuwa daga cikin kyawawan halayen da yake dasu.
Yabar bibi cikin tarin tunanin yadda wannan al’amarin zaiyiwu,sam ba batun auren hamidou bane a gabansu,batun auren mohmoud sukeyi,ta yaya za’a dauko mata abinda ba zata iya ba?.
Cikin dare MAHMOUD ya tayar da hamidou dake kukan zuci yana dubansa, murmushi ya saki
“Haba,ba’asan namiji da karaya bafa…..kada ka damu,muddin ina raye kuma hamdiyya kakeso zaka aureta”
“Ta yaya hamma?,bayan bibi har yanzun bayan wucewar abban hamdiyya batayi na’am ba?”
“Zan dosheta kuma zata fahimta” ya fadi yana duban idanun hamidou cikin bashi tabbaci.
Washegari bayan mohmoud ya gama shirin fita wajen aiki ya zauna da bibi akan maganar, hamidou yana labe ya kasa zaune ya kasa tsaye yana jiran yaji me bibi ta yanke?. Mohmoud yasha fama da ita ba kadan ba kafin tayi amanna,tsananin murna ta sanya hamidou fitowa daga inda yake laben ba tare daya shirya ba. Da kallo galala bibi ta bishi
“Ja’iri dan nema,dama kana a wajen kenan” kunya ta kamashi,ya samu waje ya zauna yana sinne kai.
“In sha Allah bibi na miki alqawarin ba zakuyi nadamar shigowar hamdiyya cikinmu ba,hamdiyya bata da wani aibu ko makusa ta fannin tarbiyya,ni kaina inda nasan da matsala bibi wallahi bazan saki jiki da lamarin ba”
“Allah yayi zabin abinda yafi alkhairi”
“Yanzun abinda na yanke hamma ya samamin wani aikin da zan dinga yi,duk sanda bamu da lecture sai na fito nayi na koma makaranta” kai mohmoud ya girgiza yana murmushi,a duniya bashi da burin da ya wuce yaga farincikin ‘yan uwansa
“Aiba wani lokaci za’a diba ba mallam,zaka tsaya tarin kudin aure kenan?,wannan yammatan yadda kuka mato akan juna banajin zata iya jiranka” kunya tadan kama hamidou amma kuma yana mamakin yadda za’a hada komai a qaramin lokaci,duk da abban yace baya buqatar komai daga wajensu face sadaki,amma ko bazai yadda ya auri hamdiyya baiyi komai cikin hidimar aurenta ba,ko yaya ne zaiyi daidai iya abinda Allah ya hore masa,a qalla dai da babu gwara ba dadi.
“Zakayi lefe kaman yadda kowanne namiji yakeyi in sha Allah,za kuma ka biya sadaki” abinda mohmoud ya fada kenan yana miqewa zai wuce wajen aiki.
Tunda yaji mohmoud ya fadi hakan yasan zai matsawa kansa ne,kuma sai yayi dukka abinda ya fada din,wannan ya sanya a sace shima ya soma ‘yan buga bugarsa,abun kamar wani yayewar lullubi sai yayita samun ayyuka,abun ya dinga bashi mamaki,saidai yayi shuru bai gayawa bibi ko hamma mohmoud ba,saboda yasan yanzun zai hanashi yace karatu kawai zaiyi,shi dinne zaiyi komai. Cikin wata guda kacal ya samu ‘yan kudadensa a hannu masu dan kauri,yanata mamakin yadda daga fara buga bugarsa qofofi suka dinga bude masa,aka dinga kiransa ayyuka daban daban da kuma kudi masu gwabi. Da yake su din damuwar danuwansu shine tasu,akwai asusu da yake yiwa oumar na jarabawar da zasuyi,wanda ya kallafawa kansa shine zai biya wannan karon hamma mohmoud ya huta shima,asusun ya bude,ga mamakinsa ya tara kudi ashe ba laifi ba kamar yadda yake tunanin bai wani tara abun arziqi ba,ya ware kudin jarrabawar oumar y dauki sauran ya hada da kudin hannunsa ya aje yana jiran dawowar hamma oumar.
A falo suke hira yana cin abinci,a kaikaicw hamidou ke kallon hamma mohmoud din saboda yadda gaba daya shekarunsa suka ninka akan nasa saboda da wahala da neman na abinci,har ya kammala mohmoud din ya kalleshi
“Ya kaketa kallo na ne kaman kaga hamdiyya?” Dariya dukka sukayi sai ya soma sude miyar hannunsa yana cewa
“Ka kwantar da hankalinka,lefenka ya gama haduwa,amma saidai su karba da haquri,akwati biyu ne” baki hamidou ya bude yana kallonsa,yayi imani ba wani lefe,lefensa ne da ya kusa shekara yana hadawa zai sadaukar masa,sai ya girgiza kai
“Aah hamma,ni bazan karba lefenka ba saboda na tabbatar shine,ni ina da kudadena da na tara”
“Kajimin yaro,yo kudadenka daka tara ai bance ba za’a karba ba,a ciki za’a fidda sadaki ka samu na dinkunan biki da dan abinda zaka bawa amarya ko bibi?” Ya fada yana maida dubansa ga bibi wadda ta kasa magana,wani irin abu me nauyi dake sauka zuciyar uwa akan danta ya tsaya mata iya wuyanta,zata iya cewa bata taba ganin mutum me tausayi da rahama ba irin mohmoud dinta,wanda ke maida matsalar wani tasa
“Haka ne,amma mohmoud kaine kafi cancanta da kakai lefen nan,ko ba komai kaine babba” murmushi yayi kawai yana nade hannun rigarshi
“Karki damu bibi,muddin kina mini addu’a tabbas zan hada wasu a kurkusa in sha Allah” daga bibi har hamidou ba wanda baiyi qwalla ba
“Yanzu gidan da zaka zauna nake qoqarin sama maka a biya haya kota shekara daya ce” mohmoud ya sake fada
“Wa?,ni?,ba inda zanje, gidanmu akwai wadatar sassa da babu kowa a ciki,a ciki zata zauna hamma ba inda zani na barku” hamidou ya fada da sauri.
Abinda suka kai sam hamdiyya ko mahaifanta basu raina ba,hakazalika ita da kanta ta qarfafi ta zauna dasu bibi din. Sashe daya cikin biyun dake cikin gidan aka bude aka yiwa dan kwaskwarima. Da yake gini ne dama asalam na masu kudin,rayuwace dai kawai data samesu sai wajen yayi kyau ya kuma dace da zaman rayuwarsu da tsarin kayan alatun da ake burin zubawa hamdiyya.
Sanda labarin aurensu ya fantsama dukka makaranta sai ta dauki dumi,saboda ba kowa keda masaniyar soyayyar dake tsakaninsu,don daga hamidou har hamdiyya kamammu ne,sun kame kansu sosai,basa wani abun da zai nuna ma akwai soyyaya tsakanin. Mazan da hamidou ya kasa suna da tarin yawa, cikin makaranta cikin nijer dama nigeria,sun kuma cizi yatsa ainun da ganin wanda hamdiyyan ta zaba ya kuma kasasu.
Biki akayi na hanakali, ba’a barnatar da dukiya ba,saidai duk abinda mohmoud ya tara saboda nashi auren ya narkar dashi gurin auren qaninsa hamidou,ya sadaukar da komai nasa ga hamidou din,ba abinda ya ragewa kansa,ya kuma tsaya ya zame masa makwafin uba mahaifi,duk abinda uba zaiyi shi yayi masa,hasalima shine alwalinsa,shi ya karba masa auren hamdiyya. Anyi biki lafiya an watse lafiya amarya kuma ta tare a dakinta.
To zamansun zama ne me dadi matuqa,duk yadda bibi da farko ta dinga dari dari da tsoron halin yaran masu wadata hamdiyya ta goge mata wannan,babu raini ko ganin ta fisu,ta sake sosai tamkar itama bibi dince mahaifiyarta. Biyayya takewa.bibi kaman yadda takewa hamidou, bashar oumar da auta dukkansu ta maidasu kaman jininta ne,ta zama dai ‘yar gida sosai,ba zaka taba cewa surukar bibi bace.
Karatunta taci gaba dayi hankali kwance,don tare suke fita da hamidou a motarta da tuni ta mallaka masa ita,saidai yaqi sakin jiki ya karba din,har zuwa sanda ya gama nasa karatun ya zama ita ta rage amma shike kaita ya kuma koma ya dauko matarsa.
Duk wasu shares da dukiya ta hamdiyya mahaifinta ya tattaro ya damqa amanarwa hamidou saboda yadda da yayi da tarbiyyarsa. Bai boye komai ba yace ga amana nan. Qememe hamidou yaqi amsa,yace zaidai aje mata takardu da kayayyakinta. Wannan qin amsar shine karon farko da suka fara samun sabani shida hamdiyya,ta dinga fushi tana cewa ya qullaci wani abune akwai a ransa game da ita ko kuma bai aminta da ita da kuma soyyayar da take masa ba dari bisa dari, Sharia har gaban hamma mohmoud da bibi,suka rasa me zasu yanke saboda su kansu ba zasuso ya cusa kansa cikin dukiyar ta ba,ko a yanzun jigila da kuma hidima take masa da kudinta da jikinta,itace cefane itace siye siyen kayan more rayuwa cikin gidan,hakanan komai ta gani ya burgeta saita siya masa. Ba shiri ya dakatar da abun
“Munyi alqawarin zaki aureni ki zauna dani daidai qarfina,bamuyi dake zakina mun hidima ba” nan ma dai haushi taji,tilas amma ta rage wasu abubuwan saboda cika umarninsa. Wannan dalili ne ya sanyashi fara neman aiki ka’in da na’in. Allah kuma cikin hikimarsa sai gashi ya jefo masa da aiki da matsakaicin albashin da yasan zai iya riqeshi da yardar Allah.
Wani lokaci abba ya kawo musu ziyara,ya kuma samu hamidou ya soma aikin nasa. Sam aikin shi bai masa ba,saboda salary din da suke basun baifi albashin qaramin ma’aikaci a kamfanin hamdiyya ba. Wannan karon da kansa ya sake neman arziqin hamidou ya dawo aiki kamfanin hamdiyya kaman hakan zaifi dacewa,ya jima yana juya abin,ya kuma gayawa bibi tace ya nema zabin Allah,sannan uwa uba mutumin surukin arziqi ne,bai kamaci ace yanata neman alfarma kala kala daga garesu suna sullubewa ba,wannan shine silar da ya fara jagorantar dukiyar hamdiyya,saidai komai yana yine cikin takatsantsan da kiyayewa,albashinsa kuma ya yankewa kansa kamar na kowa,daga gefe guda kuma ya fara saving duk wani halalinsa da yake samu silar aikin da tunanin fara shima gina kansa,saboda bazaiyiwu ace zai dawwama yana qarqashin dukiyar matarsa ba. Duk da cewa wannan abun ba abinda ya qara face soyayya me qarfi da qarin girmamawa daga wajen hamdiyyan,iya tarbiyya ta sameta,sam batasan wulaqanta dan adam ba.
Rayuwa ta fara daidaita gidan marigayi mayak’i silar wanzuwar hamdiyya a cikinsu. Abu daya ne a yanzun ya fara musu cikas shine rashin samun haihuwa shekara ta biyu da aurensu. Tun bata damu ba duk da maitar son yara da Allah ya zuba mata,to amma saboda lokacin tana cikin kai kawon karatunta har hankalinta ya fara dawowa jikinta saboda a sannan karatu ya kammala sai business dinta da takeson kamawa.
Sannu a hankali ta fara tadawa hamidou hankali,har takai anje an gwadasu,an kuma tabbatar musu mahaifar hamdiyya ce take da dan rauni. Hankalinta yayi mugun tashi duk da yadda hamidou ya nuna shi hakan ba matsala bacea wajensa,ya dinga qoqarin kwatanta mata da kwantar mata da hankali amma ta birkice masa,sun dauki watanni a haka kafin ta dan sanyawa zuciyarta salama,sai kuma zancan auren mohmoud ya taso Gadan gadan.
Haka kawai shaidan ya sanyata ta dinga jin babu dadi cikin ranta,saita dinga tsarguwa kaman za’a qaro wata surukuwar ne cikin gidan don itadin bata haihu ba. Wannan dalilin ya sanya har akayi bikin aka qare aka kawo amaryar hamma mohmoud daya sashen a tsarge take,wannan ya sanya tayi bala’in kamewa daga shiga shirgin matar hamma mohmoud.
Bintou baiwar Allah,gwanar haquri da kawaici,kyakkyawar bafulatanar katsina,wadda tasha gwagwarmayar mayar rayuwa da wahalar riqo hannun kishiyar uwar da aka fita aka bar mata. Girmama hamdiyya takeyi duk da itace matar yaya,amma tana kallon cewa ta rigata shigowa gidan,bata da hayaniya bata da magana,shuru shuru da ita kullum. Yanayin rayuwar da bibi tasan tayi ya sanyata take yawan jan bintou jikinta don ta samu ta ware ta kuma dinga jinta mutum kamar kowa. Akwai banbancin rayuwa sosai tsakaninta da hamdiyya data taso cikin gata da soyayyar dangi gaba daya. Wannan abun sai ya dinga yiwa hamdiyya ciwo kadan kadan,duk da bata taba nunawa ba amma tana jin babu dadi a ranta,tanajin kamar Bibi nason wareta ne da nuna mata banbanci don bata haihu ba,wannan yayi mata tasirin data soma janye jiki daga al’amura da yawa na gidan,ta zama ‘yar ba ruwana,dabi’ar miskilancintanan ya motsa,sai ayi abu cikin gidan ma bata sani ba,inda zakaji motsinta kawai ayi baqi yara ko ayi baqi da yara a cikinsu yanzunnan zakaga yadda zata sake jiki tayita hidimawa yaran,musamman idan akwai baby girls a ciki. Tanason ‘yar yarinya mace sosai,takancewa hamidou tafison ta haifi mace akan namiji.
Tun bibi na qoqarin fahimtarta da son fahimtar meye ya sanyata sauyawa ta nuna babu komai,har bibi ta haqura ta barta da sabon halinta,tundai ba fada takeyi da kowa ba cikin gidan,tana kuma ci gana da girmama kowa kamar yadda takeyi a baya.
Ba jimawa kwatsam ciki ya bayyana jikin bintou,yadda gidan ya rude da murna kuma kowa hankalinsa ya koma kan cikin sai ya soki zuciyar hamdiyya sosai(kusan duk macen dake neman haihuwa bata samu ba tana da shigen wannan ciwon a ranta,ko hirar haihuwa akeyi saita tsargu taga kaman da ita ake bare ace wance ai ciki ne da ita,ba wanda zai fahimci hakan sai wanda ya taba tsintar kansa a irin situation din),wannan ya sanya ta sake kame kanta da zama a sassanta ita kadai. Sai taji bata sha’awar ta rabi kowa ko wani ya rabeta,to Allah baisa cikin yana da dogon zango bama bintou tayi barinsa. Sai kuma a sannan hamdiyya ta dinga jin ba dadi,ta kuma dinga tausayin bintou, hankalinta kuma yayi mummunan tashi sanda bintou ta dinga ciwe ciwe, daga bisani gwaji ya bada cikakken bayanin bintou sicklier ce.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 07
Ta tsorata ainun hamdiyya a sannan,don mutum uku cikin familyn ummanta da taga yadda sukaci wuya da ciwon sicklier daga bisani kuma dukkansu suka rasu,wannan yayi sanadiyyar da tayi matuqar tsanar ciwon sicklier. Hatta da hamidou duk son da take masan sai da sukayi gwaji kafin aure.
Cikin hikima ta ubangiji a sannan din ashe tana maqale da cikin ALIYYU MAINA,wanda kwata kwata sam ko da alama bata sani ba bare kuma hamidou(aba). Bata tashi sanin da ciki a jikinta ba sai da yayi watanni hudu ya fara harbawa a mararta,ta tsorata dajin hakan ba shiri suka wuce asibiti. Bibi bata hanasu ba illa dariya da take musu qasan ranta, tasan yadda sukaje haka zasu dawo da borin kunyarsu.
Ilai kuwa sai gasu din,sun dawo mata shabe shabe da kukan murna da kuma kunya. Fadin yadda hamdiyya ke lele da qaunar cikin aliyyu ma kai tsaye za’a iya cewa bata baki ne, ba’a taba jarabtarta da wani abu da takeso sama da cikin ba baya ga mahaifin yaron. Motsi kadan kuma bini bini suna hanyar asibitin wai check-up a duba lafiyar yaronta,tun bibi na zuba musu idanu har ta gaji da gani ta tsawatar musu,sai suka koma fakar idanunta suna zuwa,sai kawai ta tarkatasu ta watsar.
Shirin haihuwa sukayi na garari,da ba’a qasar taso haihuwa bama amma ganin yadda bibi da bintou ke da kwadayin ganin yaron ya sanya ta haqura. Cikin aminci ta haifi aliyyu maina,sambalelen yaro da ya gaji kyau ta fannin uwa da uba da ‘yan uwan uba dinma duka. Tun asali da farinjininsa maina yazo,uwa naso uba naso qannen uba naso,hamma mohmoud kuwa ba’a ma maganarsa,don yadda yakejin haidar din har cikin jininsa,yadda yake qaunarsa da qulafucinsa har yaso ma yafi mahaifinsa. Sannu sannu tun haidar na jaririnsa sai zamansa yaso yafi qarfin hannun hamdiyya,duk da mahaukacin son da take masa. Yadda sukeson janye haidar din sai yadan fara tabata,ganin kamar ganin yaron yanaso yafi qarfinta,shayarwa ce kawai ke dawo dashi wajenta.
Cikin ikon Allah watan haidar shida uku kacal Allah ya albarkaci bintou da wani cikin,tayi murna qwarai ita da hamma mohmoud sosai. Haidar maina nada shekara guda kacal bintou ta sambalo tata yarinyar da taci sunan NAFESSA.
Da nafessa da haidar kusan duka rainon bintou suka koma,saboda tun haidar nada watanni hudun yasan idan yana kuka aka ajjiye baby nafessa a gabansa watsal watsal dinta ya dauke masa hankali ya tsaida kukan da yakeyi. Sanda ya cika shekara ta biyu kuwa yasan ya kama hanya tiryan tiryan zuwa sassansu nafessa,duk kuwa da dan banzan qyuya da yake da ita. Ya kama sunan hamma mohmoud da suke kira da pappa da kuma sunan NAFESSA daram a bakinsa fiye da sunan kowa.
Wasa wasa wata irin mahaukaciyar shaquwa ce ta shiga tsakaninsu ta yadda bacci ne kadai ke rabasu,saidai idan sunyi baccin a dauke nafessa shima a daukeshi a maida sassansu.
Alaqar dake tsakaninsa da nafessa din ta nesanta shi da ama din,tun bai isa yaye ba,tun kuma bata saba ba har ta saba. Kusan duk yininsa yana wajen bintou ne,idan kima nafessa na sashen bibi shima yana can acan zasu wuni sur saidai ya leqota. Kishin hakanne ya fara kamata ganin sannu sannu yana barin sassanta da kuma raguwar shaquwar dake tsakaninsu duk da irin qulafucinta da yakeyi. Gashi daga itan har bintou daga kan yaran ba wadda ta sake samun wani cikin,gwara bintou dama an shawarcesu da daukan dogon hutu kafin ta sake samun wani cikin saboda yanayin lalurarta, hakanan ta sha wuya sosai wajen haihuwar nafessa,nisan kwana kadai ya kawota yau. Duk yadda zata ja maina a jiki abun ya faskara,ta kuma lura ita bibi hakan yana mata dadi qwarai,tana yawaita fadin Allah ya qara hada mata kansu shi da nafessa din.
Nafessa na da shekara hudu maina nada shekara biyar alamun ciwukan sicklier suka fara bayyana a jikinta,yau ciwo gobe lafiya,qwarai bintou taso aje ayi mata gwaji amma tsoron kada ya tabbata nafessa nada sicklier hamma mohmoud ya qiya,amma dole da gumu tayi gumu ya bari akaje aka gwadata din. Ta tabbata sicklier dince kuwa, sicklier dinma irin chronic sicklier dinnan,don kuwa kwata kwata rayuwar nafessa kusan rabinta a ciwo take.
Allah ya mata halitta me sanyi,nafessa din yarinya ce me tsananin sanyin hali,shuru shuru,matuqar girmama duk wanda ya girme mata,ga tsananin son karatu kamar me?,saidai kuma karatun nata kusan rabi ne,rabin tana yinsa ne ga gadon asibiti. Duk da ana cewa sickle suna girma ciwonsu yana qara ja baya,ga nafessa abun ba haka yake ba,tana girma ciwon yana sake nuqurqusarta. Duk sanda ciwon nafessa ya tashi ba zaka iya banbance waye me ciwon ba tsakanin ita da maina. Ita kuka maina kuka,idan kaga walwalarsa to nafessa ta samu kanta. Koda bacci yakeyi muddin yaji murya ko nishin nafessa bacci ya qare masa. Abun ya sake dagawa ama hankali,tana ganin shaquwar kamar ta wuce hankali. Buqatun nafessa da hidimarta itace gaba data kowa cikin gidan,walwalarta itace tashi.
A haka shekaru suka dinga tafiya,shine komai na nafessa,shine gatan nafessa shine kuma mai tsaya mata,muddin yana wajen ba wanda ya isa ya tabata. Ya wuceta da aji daya,amma yasa aka maidashi baya ya koma ajinsu nafessa din,daga boko har islamiyya haka yayi ba tare da ama ta sani ba. Ranar data samu labari kuwa tashin hankali tayi sosai,har ta dinga ji a ranta anya wannan abun nashi na lafiya ne?. Tun nafessa nada shekara goma daga mohmoud har bintou raayinsu yazo daya na aurar da ita da wuri,saboda yanayin lalurarta suna ganin taci gaba da karatu ma kamar sun wahalar da lafiyar gangar jikinta ne.
FURUCIN da bibi tayi a wani lokaci kusan shi ya sake sanyata tsaiwa da qafafunta akan aliyyun nata. Ranar suna tasowa daga makaranta,sai ta rigashi tahowa,ashe wani ya biyota ya kuma tsaidata,maina din ya shigo gida yana cika yana batsewa, bibi tayi dariya tace
“To ko ‘yar gida za’a yi?, irin wannan kishi haka maina?” A kunnuwan ama tayi zancan,saidai bata daga kai ta kallesu ba,saidai maganar ta sauka sosai cikin zuciyar ama din,ta kuma tsaye mata a rai,daga lokacin ta fara takatsantsan da fara janye maina din daga nafessa dama harkokin gidan gaba daya,makaranta ta sake samar masa wadda zai zamana sai kusan bayan isha’i zai samu sakewa cikin gidan. A lokaci shi da nafessa din duka suna ss.2, shekara daya kawai ya rage musu su zana jarrabawar kammala secondry school.
Rashin ganin maina din kwanakin da suka biyo baya ya sanya nafessa din zuwa har sassan wajen ama nemansa,abinda ba kasafai ta fiya yinsa ba idan ba mamanta ko bibi ta aiketa ba,duk da cewa ba wani abu ama ke nuna mata ba,hasalima tana mata komai na kyautatawa kaman kayan qyale qyalen rayuwa da sauransu saboda ita daya ce mace a gidan,don ko da su oncle bashar da ocle oumar sukayi aure yara mazan suma matansu dukka suka haifa,sannan ita dinma data sake samun ciki namijin dai ta sake haufa,duk da addu’ar data dinga yi da kuma qulafucin samu diya mace data dinga yi. Haka kawai dai ba sakewa tsakaninsu,ita ama zurfin alaqar dake tsakaninsu dinne bataso,da yadda dukka haidar ya tattare tsakaninsu da kuma bibi,ita din ta zama kamar ta haifa musu shine kawai.
“Yana makaranta” kawai ama tace da ita,sai ta miqe a sanyaye ta fice. A wannan tsakanin hamani ya dawo gidan sanadiyyar karatu da ya maidoshi nan garin,hamani d’a ne ga qanin mahaifinsu aba,hamani din kamar cousin yake a wajensu. Yana da matuqar kirki da son jama’a,uwa uba matashine me addini kamewa da sanin ya kamata.
Cikin lokaci qanqani ya fara sabawa da kowa na gidan,dukka yaran idan sukaji shuru na wasu awanni basujishi ba sun shiga cigiyarsa ina oncle hamani,harda nafessa kuwa,don kusan shike mata lesson din da yanzu maina baida cikakken lokacin yi mata shi yadda suka saba a baya.
A lokacin manema suka fara zuwanma nafessa din,duk wanda zayazo gurinta ko yace yana sonta sai maina ya sani,tare suke shawarar komai.
Kusan a kowacce qasa,kuma kowacce al’umma da yawanmu suna da qyamatar auren masu lalurar sicklier,to irin wannan qalubalen ne nafessa ta fara fuskanta. Tana da kyau ainun dake jan hankalin kowanne namiji,tana da nutsuwa da kamun kai dake bawa maza sha’awa,to amma kuma da zarar sunji irin lalurarta sai ka nema mutum ka rasa. Da yake auren bai kanta da farko bata wani damu ba har sai da tafiya ta fara nisa ta fahimci qalubalen dake a gabanta,ta kuma ga zallar damuwa tattare da mommanta. A hankali ta soma fahimtar komai,ya kuma soma damunta,maina dinne dai abokin shawara da fadawa damuwarta,sai kuma oncle hamani. Duk sanda wani yazo ya tafi da maina take tattauna damuwarta
“To sai meye?,yayita tafiya,Allah zai kawo miki wanda ya fishi” duk sanda ya fadi hakan hankalinta yana kwanciya sosai.
Ranar da zuciyarta ta karye sosai ranar da wani hafizzou ya shaida mata soyayyarsu ba zata iya ci gaba ba. Shigowar maina gidan kenan daga makarantar manya ta dare,yaga fitar hafizzou ya kuma ga shigewar nafessa ciki da sassarfa sassan bibi,sai kawai ya take mata baya yana addu’ar Allah yasa bame afkuwa bace ta auku.
Yana shiga ya sameta saman cinyar bibi din tana sharba kuka. Aba na falon haka haka ama,suna list na abubuwan da bibin keso ama zata taho mata dasu daga Nigeria,don saura kwana uku ta wuce can din,kasancewar bata rabo da zuwa don suna da tamfatsetsen gida a can da idan sunso suna iya share wata uku ciki kafin su dawo niger,ita da aba ko ita daya dinma.
“To sai meye?,a kansu kike zubda hawayenki nafessa?,suyita tafiya din,ni zan aureki,na yarda ni aliyyu zan aureki” ya fada cikin tsanani fushi da zafin zuciya. Ba ama kadai maganar ta yiwa luguden duka ba,har bibi da ita kanta nafessa din. Dif falon yayi abinda maina bai tsaya wani la’akari dashi ba yaci gaba da zazzaga masifa.
Sakale ama kawai tayi tana kallon ikon Allah kuma zatonta yana sake qarfafa lallai aliyyun wasu ta haifawa. Zuciyarta ta gaza daurewa ta daka masa tsawa me qarfi
“Yima mutane shuru dalla,shashasha!,fita ka bawa mutane guri” ta fadi a harzuqe. Har ya fitan suka gama abinda sukeyi ta fice itama babu wanda yace komai akan maganar.
Cikin kwanakin ukun tanata shirin tafiya Nigeria amma ranta a matse yake,gaba daya ta rasa walwalarta,hatta aba da maina sunga canzawarta,tanata juya furucin maina a ranta,tana kuma hankalce da yadda suketa dan shige da fice a sassan bibin lokaci zuwa lokaci. Bataji koda d’ar ba,saboda ta riga ta sama ranta ko sama da qasa zasu hade ba zata yarda maina ya auri nafessa ba,abumma sam bai kama hankali ba,ko ita da mahaifinsa da sukayi aure duniya nada ragowar kwanciya ai dukkansu sai da suka mallaki hankalin kansu sannan sukayi,uwa uba ma kuma bataga dalilin da zai sanya ta bari maina din data dora buri a kansa ya auri sicklier ba,duk da nafessa bata da matsala ko makusa tako ta ina,amma abun ita sam bai kama zuciyarta bama bare hankalinta.
Haka ta tattara harda maina din suka wuce Nigeria,abinda yasa ta gane da wani abun a qasa,tun sanda zasu taho basuyi sallama da aba ba yadda suka saba,sannan a qa’ida tare suka tsara zasu tafin amma shi ya janye tashi tafiyar,bataji dadi ba amma ko a jikinta suka wuce din.
Sanda ta kammala kwanakin data diba zatayin sai taji kwata kwata bata sha’awar komawa nijer,tayi zamanta a nan din duk da lura da tayi maina ya takura su koma din. Suna hutu ne a sannan,kuma hutunsu yakan dauki dogon zango wani lokaci wata uku har hudu ma,ba guntun hutu irin namu ba,wannan ya sanya ta sake miqe qafa,tayi biris kamar bata karanci damuwarsa ba.
Sati guda ta qara akan ainihin kwanakinta aba yayi mata dirar mikiya. Hakanan kadaran kadaham babu wannan karsashin kamar yadda suka saba. Kwana daya kwana biyu shuru,a kwana na ukun suna breakfast da safe ya dubeta yana gaya mata labarin da ta jishi kamar saukar aradu
“Mun yanke shawarar daura auren maina da nafessa” a wani hargitse ta dago tana dubansa
“Wanne maina din?,kana nufin aliyyu haidar?,wanda ko qaramar secondry bai gama ba?dududu shekarar haidar din nawa?,,baya ga haka ka manta nafessa sa’arsa ce?,watanni sha biyu kacal ya bata?,ka manta matakin lafiyarta?”
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 08
“Dukka wadannan lissafinki ne,ba ruwana dasu” ya furta cikin halin ko in kula.
Wannan magana ita tayi silar kawo rikicewar familyn MAYAK’I a karon farko,ta nesanta zazzafar soyayyar dake tsakanin aba da ama me matuqar danqo,soyayyar da bibi bata taba sasanci ba a tsakaninsu,saboda ba qarya hamdiyya ta iya riqon miji qwarai da gaske.
Batayi qasa a gwiwa ba ta yanki tikitin komawa nijer saboda ta tabbatar ba shi daya yayi wannan shawarar ba. Ta dire gaban bibi takuma lissafa mata dukka hujjojinta na rashin amincewa da batun auren maina da nafessa. Bibi din jinjina kai kawai tayi, bata fidda matsayarta ba,don a duniya ba wanda zai kaita son ganin maina da nafessa qarqashin inuwa guda.
Ganin yadda abubuwa keta rikicewa cikin gidan ya sanya oncle mohmoud wanda tunda aka fara lamarin har sanda su bibi suka yanke hada auren bai taba magana ba sai yanzu ya gurfana gaban bibi yace yana roqon alfarmar abar wannan batun,ko don hamidou ya samu zaman lafiya da iyalansa,maina kuma ya samu albarkar mahaifiyarsa. Kai da fata aba yace shifa baisan zance ba,ya riga ya bawa maina nafessa,babu kuma fashi, saidai hamdiyya tabar aurensa.
Sosai maganar ta taba bibi,salin alin ta kwabeshi itama,tace kuma an janye maganar. Kamar jira hamani yakeyi yace shi zaya auri nafessa. Ba wanda ya qyamaci abun a cikinsu,saboda hamani din managarcin mutum ne,kuma dama can shi bame kule kule bane,hasalima babu wata yarinya da yake nema. Dai dai sanda ya kammala Phd dinsa daidai sanda nafessa ta kammala secondry school,babu jinkiri aka gabatar da komai,aba ya daure qarqashi akayi gagarumin biki, Wanda kamar ama tasan za’a yi hakan ta saka maina a gaba suka wuce Nigeria.
Tunda suka tafi din bai dawo nijer ba,hasalima sai ya fara neman gurbin karatu a can,don baijin zai dawo nijer kuma rayuwa taci gaba da gudanar masa kamar yadda yakeso. duk da yayi murna qwarai da nafessa ta samu mutum kamar hamani,yayi imani ba ita babu kuka saboda nagarta da kyan zuciyarsa.
Duka duka auren nafessa watanni shida,tana da ciki wata hudu bintou mahaifiyarta ta rasu. Mutuwar ta girgiza ta ta kuma jijjiga mohmoud,saboda shi kadai yasan irin macen da Allah ya bashi. Albarkacin samun nagartaccen miji dukan mutuwar yazo mata da sassauci,ya tsaya kai da fata ganin matarsa bata fuskanci raurawa ba.
Watanni uku da kwana goma nafessa ta haifi SULTANA, yarinyar da ta samu soyayyar da har ta dara wadda mahaifinta da kuma maina din ya samu,yarinyar data debo kamannin NADEEYA abinda ya qara adadin soyayyarta a zuciyar kowa da kowa. A sannan tuni dukiya ta fara yiwa aba ambaliya,ya fara shiga jerin sahun attajiran ‘yan kasuwa masu cin gashin kansu,don bai jima da dukiyar ama a hannunsa ba ya damqa mata komai ya dorata akan turba ya kuma bata cikakken damar kula da dukiyarta kamar yadda kowanne namiji zaiyi shi kuma ya waiwayi tasa.
Iya bikin suna kawai kudade aba ya zuba masu ciwo yace ayi,duk da hamanin ma ba baya bane gurin samu,don tun yana lavel one a jami’a ya fara kasuwanci,kawo yanzu kuwa shima ya zama babban qwaro. Gata iya gata ta kowanne fanni. Ga hamma MAHMOUD jin sultana yake kamar wani yanki na jikinsa, soyayyarta bata taba boyuwa muddin zaka zauna dashi koda na minti talatinne. Ya zubawa sultana so wani irin so me tsayawa a zuciya tun tana zanin goyonta. A haka aka fara rainonta kafin me afkuwa ta afku,mutuwa ta rabata da mahaifiyarta nafessa.
Mutuwar ta daki maina matuqa ta kuma galabaitar dashi,sai kuma a lokacin mutuwar ne ya fara dora idanunsa akan sultana da a sannan take koyon zama watanni uku da kwanaki a duniya.
Wani irin masifaffen so ya azawa sultana,bama shi kadai ba kusan kowa na cikin gidan,yana ji a ransa kamar yanzun sultana responsibility nasa ce,kamar shike da alhakin komai nata. Rasuwar nafessa da samuwar sultana ya sanyashi ajjiye karatunsa ya dawo gida nijer. A hannunsa sultana ta taso,ya zama shine uwa kuma shine uba a gareta,tsarkin kashi wanka raino rashin lafiyarta dama walwalarta dukka na hannun maina. Maina ta budi idanu ta gani a matsayin uwarta kuma ubanta tun gabanin ma hamani da hamma mohmoud din suma subi bayan nafessa sanadiyyar hatsarin motar da suka samu shi da shi a hanyarsu ta dawowa daga ziyarar kabarin nafessa din. Wannan maraicin da sultana ta sake tsunduma ya sake ninka soyayyarta,ya kuma sanyashi sake ninka kulawarsa ninkim baninkin a kan sultana,ya ajjiye karatunsa gaba daya saboda ita,wasu abubuwan tun bai iya ba har ya qware sosai,hatta jakar goyon sultana yana da ita,yadda yarinyar ta taso tana qulafucinsa sai ya masa kamanceceniya da mahaifiyarta. Ta dabance sultana cikin gidan kamar yadda komai nata ya zama na daban,tana da farinjinin da kowa ya shigo sai ya dauketa ko ya tankata,tana da yawan surutu tun shekarunta suna qananu ainun,tana da kazar kazar irin ta masu cikakken lafiya.
Halasci da sadaukarwar mohmoud ba abune qanqani ba da zaiyi saurin bacewa zukatansu ba,ba qaramin abu bane da zaiyi saurin shafewa a rayuwarsu ba,a wajen aba hamma mohmoud din uba ne wanda yayi masa komai a rayuwa,bashi da abinda zai saka masa dashi face ya bawa jininsa qwaya daya tal da ya bari a duniya dukkan soyayya qauna da kulawa,wannan ta sanya ya fifita sultana akan kowa cikin gidan,buqatarta ta zama gaba akan buqatar kowa.
Ya koma makaranta a nan maradi amma saboda hankalinsa nakan rainon sultana sai karatun nasa ya zamana asha ruwan tsuntsaye ne,yaqi ya maida hankalinsa duk da karatunsa karatu ne me tsada da wahalar samu,yake kuma da buqatar maida hankali akai. Aba da kansa da ya fahimci muddin yana tare dasu ba karatun zaiyi ba,sai ya maidashi niamy,ya tafi kuma da sharadin sai yayi shekara cur aba yaga kamun ludayin karatunsa sannan zai barshi ya fara zuwa gida weekend. Itadai ama bata tanka ba,don zuwa sannan ta zama ‘yar don’t care game da komai na cikin gidan,ba komai take sanya baki ba duk da dama ba halinta bane shishshigi,sa’annan har kawo yau aba zafinta yakeji akan hana auren maina da nafessa. Dukka tulin soyayya da suke nunawa sultana bataga aibu ba,don sultana din jinin mohmoud ce, MAHMOUD kuma abun asoshi ne,ko ita yana daya daga cikin mutane masu muhimmanci cikin rayuwarta,abu daya ne ta dinga jiye musu wanda a yanzun ya riskesu,sangarcewa da lalacewar tarbiyyar da maina keta fadi tashin ganin tafi kowanne yaro cikin gidan,abinda ta dinga gane musu kenan,amma taja bakinta tayi shuru don tasan ba muhallin da zatayi magana bane,don ba lallai su fahimceta ba. Kaf yaran gidan ita kanta sultana din tafi shiga ranta,tana tausayinta saboda maraicin da take ciki ta kowacce fuska,amma hakanan ta barma ranta hakan saboda a qalla dai a samu wanda koda da kallo zaya nuna mata kuskure idan ta aiwatar cikin gidan,sannan ba lallai su gamsu da ita ba wai don ta nuna tana qaunarta,duk da cewa tasan kusan komai ya riga ya wuce,family ne da basa da riqo sam sam sam,daya daga cikin halayensu dake burgeta.
Sanda ya cika shekara ya fara zuwa gidan bai fahimta wani sauyi sosai daga gareta ba. Saidai bahaushe yace sannu sannu hata hana zuwa saidai a dade ba’a je ba, shekara guda da fara zuwan nasa ya karanci komai,hankalinsa ya dagu sosai,yayi iya bakin dukka qoqarinsa wajen saita komai amma inaaaa……wannan shine ya zama SILA kuma SANADIN KADDARAR data samesu a yanzu………KADDARAR da zata budewa SULTANA da MAINA qofofi masu tarin yawa…..
Barkanmu da sauka😄,muje zuwa guwa ga tsakiyar labarin🤩
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 09
Numfashi me nauyi ama ta aje tana sake murza tafin hannun sulatana dake tsakiyar hannunta wanda ya sake yayi laushi sosai
“Ya hayyu ya qayyumu birahmtika astageesu” ta furta qasa qasa tana lumshe idanuwanta. Batasan me qaddara ta tanadarwa gobensu ba gaba daya,saidai ko meye tana fatan yazo ya wuce sa gaggawa,ko meye kuma tana fatan yazo ya wuce musu cikin sauqi.
Hannunta ta saje miqawa ta jawo wayarta tana sake lalubar number wayar maina,har yanzu akwai dacinsa da ciwonsa qasan zuciyarta,tana sake jaddadawa kanta da gayawa kanta ba zata masa ta sauqi ba,ba zata kuma sassauta masa ba dole tayi masa mafi munin hukunci,saboda ba haka takeso ya rayu da nashi iyalin ba,ba haka takeso ya soma gina rayuwarsa data zuri’arsa ba,tana da buqatar tsatso me kyau wankakke daga wajensa tamkar yadda ahali da salsalar mahaifinsa suka kasance.
Babu wani abu da ya canza,har yanzu dai gaya mata akeyi wayar na a kashe ne. Furzar da iska tayi daga bakinta tana sake gayawa kanta duk nisan kiwon da yayi zaije ya dawo ya sameta.
Sai data duba lokaci taga yadda dare yaketa sake nisa sannan ta fidda hannunta daga na sultana,ta miqe ta zare yalwataccen mayafinta da kowanne motsi yake fidda qasaitaccen qamshi. Toilet ta shiga ta dauro alwala don batajin zata iya samun bacci,ta shimfida darduma ta tada salla.
Raka’a shida tayi ta sallame,ta bude ipad dinta tana buda app na qur’ani cikin nutsuwa ta soma karantawa ko zuciyarta zatayi sanyi daga abinda takeji.
Duk bayan kowannw minti sai ta aza idanunta akan sultana da har yanzu jiya iyau. Tayi nisa takai gwargwadon izifi biyu ta sake dora idanunta akan sultana,sai taga hannunta da qafafunta suna wani irin motsi kamar ana jijjigasu.
Da hanzari ta aje qur’anin ta kuma miqe tana nufarta da sassarfa,dab da zata isa inda take sultana din ta soma fusge fusge kamar wadda aljanu suka yiwa mummunan kamu,kafin daga bisani ihu ya biyo baya da dakusashiyar muryarta data fara budewa. Gaba daya gigicewa ama tayi da irin abinda taga sultana din tanayi,sosai take jijjiga tana kuma ihu tare da kiran sunan maina kaika dauka wasu gaggan mayu ne suka kamata. Rungumeta tayi sosai a jikinta gudun kada ta farke dinkin jikinta ko ta jiwa kanta rauni,tana rungume da ita din tana kiran sunanta,saidai bisa dukkan alamu bata fahimtar ma abinda takeyi bare wanda ke kusa da ita,abinda ya sanya hawayen tsananin tausayinta ya sauka a idanun ama. Tanason ta matsa gaban abun kira ta kirayi nurses amma tana tsoron sakin sultana din,cikin taimakon Allah kamar Dr chafa’atou tasan halin da ake ciki sai gata ta turo qofar dakin ita da Dr cha’aibou.
Hannuwanta dake cikin aljihun labcoat dinta ta zare tana nufosu da gaggawa
“Ta farka ne?” Ta tambayi ama tana tayata riqe sultana
“Ta farka Dr amma a mafi munin yanayi” ta bata amsa tana qoqarin dauke qwallar data sauka saman idanunta. Dr cha’aibou ta yiwa magana ya qaraso ta sanyashi ya duba allura cikin drawer din da suka ajjiye dukka tarkacen allura ruwa da magungunan da sukasan ciwonta yana da buqata.
Shi ya hada allurar ya kuma yi mata. A hankali sai yanayinta ya fara daidaita,saidai kuma dukka jikinta ya fara sakewa,kafin daga bisani ta sake komawa wani baccin.
Shuru dakin ya dauka idanunsu dukka a kanta,kafin daga bisani Dr chafa’atou ta furzar da iska tana maida dubanta ga ama
“Dole zata hadu da attack dama irin wanda aka yiwa rape suke haduwa dashi,saboda wannan abun da akayi matan kusan daidai yake da rape a tunani da kuma qwaqwalwarta,tunda anyi shine bisa qarfi da tilastawa,kwanyarta sam batasan meye sahihin ma’anar aure ba bare ta banbance,amma in sha Allah ina saka ran idan ta sake farkawa zata farka babu dukka wadannan abubuwan,ki kula da kyau don ba dogon bacci zatayi kamar irin wannan data fark daga shi ba,ko na turo miki nurse hajja ta tayaki zama?” Kai ama ta girgiza a sanyaye,bata buqatar kowa ya tayata tunkarar wannan,bata da buqatar wani ya aboceta cikin wannan lamarin,tanason ta tunkari komai ita daya da zuciya da gangar jiki irin ta UWA.
Tunda Dr chafa’atou ta fadi haka ta tattara ta dawo gaban gadon ta tare,qarfe biyu qarfe uku qarfe hudu dukka saman idanunta suka wuce,bacci ko gezau baibi ta kusa da ita ba bare ya gwada daukarta,har zuwa sanda sanyin dake bayyana gabatowar asuba ya soma busawa,a sannan sultana din ta fara bude idanunta a karo na biyu,wannan lokacin cikin nutsuwa,saidai kuma tana jin dukka jikinta wani iri babu dadi,sannan daya idon nata kuma yaqi bude mata da kyau yadda takeso. Jin hakan ya sanyata daga hannu da niyyar shafa fuskar taji me ya hanawa idon nata budewa da ganin abu da kyau. Riqe hannun nata ama tayi da sauri tana fadin
“Bari karki goce qarin ruwan” a nutse ta waiwayo gefanta,idanunta suka sauka kan fuskar ama din,a hankali kwanyarta ta fara tuna mata abinda ya faru da ita na qarshe. Tunanin da ya sake hargitsata karon farko cikin hayyacinta,sai wani irin nannauyan kuka me sauti ya kufce mata.
Tana iya tuna sanda maina ya tsiraitata ya yage kowanne tufafi dake jikinta,tana iya tuna sanda hannuwansa ke kaiwa guraren da ita kanta tana kyautata zaton ma qilan bata taba tabawa ba,tana iya tuna sanda lokacin da ya sadar da kansa da wajen da ko kallonsa bata yi duk da a jikinta yake……wani kukan ya sake qwace mata me matuqar sauti fiye dana baya,sai dukka wani qarfin hali da qwarin gwiwar ama ya kwaranye,ta rungume sultana din sosai a jikinta tana lallashinta.
Sun jima a haka kafin kukan nata ya ragu,sai ta koma sauke ajiyar zuciya kafin ta bude bakinta cikin hardewar harshe tace
“Ruwa” sakinta ama tayi ta bude carton din ruwan dake aje gefe ta ciro guda daya ta hado da glass cup din da aka shirya a wata qaramar cabinet a dakin. Ajjiuesu tayi a gefe sannan ta fara qoqarin tadata zaune don taji dadin shan ruwa. Siririyar qara sultana ta saki tana runtse ido saboda azabar da taji na ratsata,kowacce gaba ta jikinta ciwo takeyi mata
“Sannu,daure kisha ruwan sai na saka ruwan dumi na gasa miki jikinki ko?” Ama ta fadi a tausashe tana kallon qwayar idanun sultana cikin matuqar tausayin ta shigo stage din da bai kamata ce ta shigo shi ba.
Tana qananun qwalla tana komai ama ta tada ta,ta zuba mata ruwan ta shanye ta kuma sake buqatar wani,haka ta dinga zuba mata tana shanyewa har sai da tasha rabin gorar sannan tace ta qoshi.
Da kanta ama ta tara ruwa me dumi qwarai ta dawo cikin dakin
“Muje ki wanke jikinki ko zakiji dadi” a hankali sultana ta kauda kanta gefe kadan tana jin zuciyarta kamar zata fashe,ganin ama kawai tuna mata yake da maina da abinda ya aikata mata,wai shin ta yaya zata iya ci gaba da kallon ama?,ta yaya zata iya tubewa ama jikinta tayi mata wanka?. Mutum biyu rak a rayuwarta suke mata hakan,daga bibi sai tanja,batajin akwai sakewa tsakaninta da ama da har hakan zata kasance
“Ina bibi ta?” Ta tambaya cikin rauni ba tare data Kali ama ba
“Suna gida,dare yayi yanzunma asuba ce,amma goben nasan da sassafe zaki ganta”
“Zata yimin idan tazo” tace da ama tana jin kamar harshenta take yanka a duk sanda ta buda baki tayi magana,saboda sam sam a yanzun furta kowacce kalma ta daina bata sha’awa,tafi sha’awar kurumtaka da bebantaka akan komai,batason jin duk wani sauti ko kuma kalma bare ta tuna mata da ALIYYU MAINA.
Tsaiwa ama tayi kawai tana nazarinta,har yanzu taqi waiwayowa bare ta dubeta,sai ta taka a hankali ta isa sashen data maida kanta ta zauna,ta jawo hannunta ta saka cikin nata
“Sultana?” Ta kirata kiran da ya ratsa mata jiki,ta kuma daga kumburarrun idanunta da dayan bai iya gani da kyau ta kalli ama sannan ta maida dubanta qasa
“Inason ki daukeni daga yau a matsayin bintou mahaifiyarki da baki santa ba,inaso daga yau ki sanya a ranki ni ba babar maina bace,ban haifi d’a aliyyu ba,ke kadai na haifa,zaki iya daukata a matsayin mamarki da zaki iya gayawa dukka damuwarki?” Kiran sunan maina din ya saukar mata da wani zafi daga zuciyarta,amma kuma data dubi ama saita tuna cewar…….matar bata taba takura mata ba,bata taba shiga huruminta ba bare ta dameta ko ta hantareta cikin gidan yadda sauran matan kawunnanta suke mata,bata taba mata wata mummunar magana ba,hasalima ko meye zatayi ba ita cikin masu yi mata caaa. Abinda kuma ta gani idanun ama din a sannan yayi kama da abinda d’a yake gani cikin idanun mahaifiya,haka kawai taji wata nutsuwa ta saukar mata tattare da ama din,bata daice mata komai ba,amma kuma bata sake musawa ba,ta kamata ta kaita bandakin ta kuma fara yi mata dukkan wani abu da tasan zai sanya taji dadi cikin jikinta,cikin hikima kuma tana shaida mata ciwukan dake jikinta don kada tayi wani abu me qarfi da zai kawo matsala a wajen.
Abun yayi mugun yi mata banbarakwai tare da daure mata kai,dinki a wajen hanyar fitsarinta?, tabbas kasheta kawai maina yaso yi,bata taba gani ko jin an dinke wajen ba,sai qwalla ta cika mata idanu ta kuma ga gangaro tabi ta saman kuncinta ta hade da ruwan wankan dake a jikinta,dama koda ama bata gaya mata ba tasan wajen ba lafiya yake ba,don ita kadai tasan yadda taji gurin yayi mata,tanajin kamar ba’a jikinta yake ba,zallar radadi da zugin da yake mata ne kadai yake tabbatar mata a jikinta har yanzu yake.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 10
Kuka sosai ta sakarwa ama saboda kalar azabar da takeji sanda ama din ke gasa mata jikinta. Tausayinta ya cika zuciyar ama din fal,kamar ta zauna itama tayita mata kuka ko ta barta kawai taji da ciwukan jikinta,saidai kuma hakan ba zaya yiwu ba,gatan da zata mata kenan hakan kuma shine zai sanyata ta warware da wuri. Itama ama din bata hanata kukan ba,tana ganin idan tace tayi shuru ko kada tayi kuka bata yi mata adalci ba,aika aikar da maina din yayi mata ko uwar mata ce ita sai taji jiki,bare yarinyar da har yanzu rainonta akeyi.
Tsaf ta wanketa ta lullubeta da towel,ta kuma riqeta cikin takatsantsan suka dawo cikin dakin ta tayata ta shirya,ta fidda simple gown cikin kayanta ta bata tace ta saka,sannan ama din ta matsa gaban kayan tea dake jere ta fara hadawa sultanar wadda tunda ta gama shiryawa ta maida idanunta ta kulle. Gaba daya ji takeyi ko duniyar batason kalla,yanzun waye da waye yasan abinda maina yayi mata?,me zata cewa mutane?,da wanne ido zata kalli ‘yan gidansu?,qawayenta dama ‘yan unguwarsu?,me ta yiwa maina haka daya gwammaci ya kasheta ya huta?,bata taba zato ko tsammanin zata farka ta ganta cikin gidan duniya ba.
“Tashi kisha sultana” ama data gama hadawa ta dawo ta zauna gefanta ta fadi cikin salon lallashi. Bata iya bude qullallun danunta da hawaye ke ratsasu yana fitowa ba ta girgizawa ama din kai. Batajin akwai wani abu me sunan abinci da zaya isha shiga cikinta,sam ita bata sha’awar komai ma koda kuwa ruwa don ya zame mata dole ne ta karba a dazun ta sha.
Duk yadda ama ke tunanin zata lallabeta ta karba tea din amma ta qiya,daga bisani ma daina amsawa ama din tayi,sai ta koma kamar wadda bacci ya dauka,dole ama ta mayar ta aje,saita koma kujerar dake fuskantar sultana din tana nazarinta lokaci lokaci,yayin da wani kaso na hankalinta ya tafi ga ci gaba da karatun qur’aninta ko zata samu sassauci cikin zuciyarta,ta wani bangaren kuma bata gaji ba hakanan bata sare ba da gwada kiran wayar maina,amma dai duka sammakal,ba abinda ya sauya,wayarsa a kashe take.
Kafin a kirayi sallar asuba baccin gaske ya sake daukar sultana,wani irin wahalallen bacci da babu armashi ko karsashi ko kadan a cikinsa. Gyara mata kwanciya kawai tayi ba tare data tasheta ba,ta wuce bandaki tayi wanka ta hado da alwala sannan ta dawo ta tada salla.
Sallamarta daga sallah yayi dai dai da shigowar aba,ta bishi da kallon mamaki,tamkar wanda baiyi sallar asuba ba?,ko kuma a nan cikin asibitin yayi?,tafi zaton hakan,don fuskarsa batayi kama da fuskar wanda ya tashi daga bacci yanzu ba,tafi kama da fuskar mutumin da bai samu cikakken bacci ba.
Da sallamarsa ya shigo,fuskarnan sam babu walwala ko ta gamun gafara sai tarin damuwa da firgici. Kujera yaja gefan gadon sultanan dake bacci,ama tayi qoqarin shafa addu’arta cikin rashin qwarin gwiwa ta soma gaidashi. Gaisuwa daya rak ya amsa mata yabiyo bayanta da tambayar
“Yaya ta kwana?”
“Gata nan alhamdulillah”
“Da sauqi jikin nata?” Ya sake jefawa ama tambayar kai tsaye
“Eh,da sauqi,don har nayi mata wanka”
“Yaushe likita zai shigo?” Ya kuma tambaya yatsunsa harda cikin na juna
“Basa wuce shida na safe” sai ya jinjina kai kawai,bai sake cewa komai ba ya zaro wayarsa ya soma gwada kiran wata number. Bugu biyu ta shiga ya soma magana da wanda ya daga kiran
“Inason ayi cancel tafiyar nan,a maidata sati na sama…..eh yau din gobe dama jibi duka ina da wani uzuri….. okay yayi Allah ya kaimu” ya fadi qasa qasa.
Maganar da taji aba din yanayi shi ya tuna mata da shirin tafiyarta Nigeria wanda da a yau zata yishi,sam wannan abun ya sanya ta manta da komai,sai ta ciro wayarta tana dubawa.
Tarin miscal ta gani na masu aikin gidanta na nigeria,musamman bilki miscals dinta yafi na kowa yawa,sai kuma miscal din yayanta. Dukkansu tasan kowa yanason yaji qarfe nawa ne zata sauka,ta duba lokaci har yanzu a biyar da rabi suke,idan ta kira yaaya din a daidai lokacin yayi safiya da yawa,tunda ko banza me iyali ne shi,don haka saita soma kiran bilki.
Dab da zata katse ta daga tana fadi cikin girmamawa
“Afuwa hajiya,bacci ne ya daukeni bayan na idar da sallah,ina kwana?”
“Lafiya lau bilki”ta amsa mata cikin rashin karsashi
“Yauwa dama inata son naji qarfe nawa zaki sauka don nasan me za’a tanadar miki,don tun jiya an gama kintsa gidan,me gyaran batiran inverter dinnan ne kawai bai iso ba,amma shima yace qarfe bakwai na safiya zai shigo” Boyayyen numfashi ta saki
“Ya taho a nutse,kada kuma ku dora komai saboda ni,tafiyar nan ba yau ba”
“Toh hajiya,sai gobe kenan?”
“Ba gobe ba kuma jibi ba,kawai duk sanda na shirya sake zuwan zai sanar muku”
“To hajiya,Allah yasa lafiya,Allah ya bamu aron rai”
“Ameen” kawai ama ta amsa mata tana gimtse kiran.
Yadda dakin yayi shuru da yawa saita kasa sakewa,haka kawai takejin wani iri,daga ita har aba kalma daya game da ciwon nata hadasu ba wai da zummar tattauna,batasan inda ya dosa ba ko kuma me yake saqawa a ransa ba,sai kawai ta buge da danna wayarta,wanda ita kanta batasan me takeyi ba,kafin daga qarshe ta shiga sms ta soma rubutawa maina gajeran saqo ta number wayarsa
“Duk inda kake kada ka kuskura kakai dare baka dawo gida ba,wannan din umarnina ne” . Abinda ta rubuta masa kenan a gajarce ta tura masa.
Qofar aka taba sannan kuma aka murdata aka bude. Dr chafa’atou ce sanye da kayan gida,kai bazaka taba cewa likita bace ita din. Da alamu sammako itama tayi,kuma duk yadda akayi ta kwana da abunne itama cikin ranta.
Cikin girmama juna suka gaisa,ta gaida aba cikin matuqar girmamawa shima,sannan ta fara duba sultana din tana yiwa ama tambayoyin yadda suka kwana. Tun sanda Dr chafa’atou ta shigo sultana ta farka,amma data fahimci ba su kadai bane cikin dakin harda aba sai ta kasa bude idanunta,saidai kukanta data dora ta hanyar fidda qwalla,wanda sam basu lura ba sai da Dr chafa’atou tasa hannu ta juyo da fuskarta tanason ganin yanayin idanunta.
Ta fahimci ta farka kuma kuka takeyi,sai kawai ta yagi tissue tana goge mata hawayen cikin takatsantsan din kada ta fama mata fuskarta,tasan tana tsananin yanayin da take ciki,so ba buqatar ayi maganar da zata ji ta takura ko a tilasta mata boye damuwarta ko don gudun kamuwa da depression da tayi imanin indai ba’a yi da gaske ba tana iya tsintar kanta a ciki muddin ba’a kula da kyau ba
“Dr ina fata komai lafiya” aba ya tambayi Dr chafa’atou kai tsaye. Sai data dan juyo kadan ta kalleshi sannan ta maida dubanta ga fuskar sultana
“Eh lafiya alhamdulillah,saidai idanun nan nata inajin anjima kadan sai an dubashi sosai,don yaqi sauka daga kumburin da yayi,sannan da alama ma kamar bata iya budashi da kyau ma ko?” Tayi tambayar tana me neman amsa daga wajen ama. Kai aman ta gyada mata tana bata tabbaci.
“Oh…..bayan abinda ya aikata kuma har sai daya hada da illatamin idanun yarinya?” Aba ya fadi da wani irin tune,wanda sai a yanzu ta gama fahimtar inda aba ya sanya gaba akan case din.
“Ba matsala in sha Allah” Dr chafa’atou ta fadi don ta kwantar masa da hankali. Kai ya jinjina da qarfin gaske hannayensa zube a aljihun wandonsa
“Kuyi mata cikakken bincike,idan da wani matsala inaga zaifi kyau ku bani ita na fita da ita waje ayi mata dukkan abinda ya kamata” Ya fadi yana hadiye wani abu me daci dake taso masa,tsantsar tausayin yarinyar da kuma rashin imanin maina qarara yana bayyana a idanuwansa.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA*
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 11
“karka damu alhaji,in sha Allah zamuyi duka bakin qoqarinmu” kai kawai ya jinjina sannan ya waiwaya yana duban ama
“Na kirashi yafi sau shurin masaki ban sameshi ba,ban sani bama ko blocking dina yayi?,me yiwuwa tunda ke uwarsa ce bazai iya miki haka ba,idan kin sameshi ki shaida masa saqon da yabar mana ya riskemu,munga result kuma a qasa mun gode” daga wannan ya sanya kai ya fice,sai ama ta bishi da kallo baki sake. Me aba yake nufi ne?,baisan yadda suke nemansa itama hakan bane,ta kirayeshi bata sameshi ba?,sannan tayi zaton zaiyi maganar ya dawo gida ne ya karbi hukuncin da ya dace dashi,a maimakon hakan sai taji wata magana ma yakeyi daban wadda a nata ganin a yanzun ba nanata maganar bane ya kamata a dinga yi,abinda yafi kyau shine asan meye abu na gaba da ya kamata ace an aiwatar.
K’arfe bakwai da rabi sai ga bibi an kawota,ita da matar oncle umar. Jikinta sanye da lallausar bubu cotton ‘yar saudiyya,hannunta riqe da casbahar da kana gani kasan itama ita ta kwana ja. Dukkansu suna a gaban gadon sultanar suna mata sannu,saidai ba wanda ta tankawa,hasalima ko qwayar idanuntan taqi ta bude ta kalli koda bibi dinne,sai hawaye da suke bulbulowa ta qasan idanun. Juyin duniya bibi tayi ta bude ido amma ta qiya,duk da dama daya idon ba wani buduwa yakeyi sosai ba,koda ta bude dinma bawai ganin komai tarwai takeyi ba.
Da bibin ta gaji ta koma lallabata ta tashi taci abinci,abincin da tafiso ta sanya tanja ta dafa mata tun sassafe,shima har bibi din tayi ta gama bata ko motsa ba bare ta nuna tasan me sukeyi,daga qarshe ma sai ta gyara kwanciyarta ta basu baya ta fuskanci bango sanda ‘yan dubiya suka fara isowa dakin.
Ita daya tasan me takeji cikin zuciyarta,wani baqinciki da wani abu me tauri ne tokare tsakiyar maqoshinta. Kunyar kallon kowa takeji,hakanan kuma haushin kowa takeji. Ta tabbatar inda bibi bata biyewa umarninsa ba ta sakata a gaba sun tafi yadda suka saba da yanzun babu abinda ya sameta. Kusan ta tarkata dukka laifin ne ta azawa bibin,tana ganin sassaucin da ta yiwa maina dinne har ya samu qofar aiwatar da mummunar nufinsa a kanta.
Wasa wasa sai gashi takai har qarfe biyu na rana bataci komai ba,maganinta ma babu wanda tasha a ciki sai uban kuka data saka gaba. Duk wani motsin sultana din yana kan idanun ama,a yanzun tana sake jinta ne kamar saddi,tana ji kuma har cikin rai da zuciyarta nauyinta ce sultana,dolenta ce sultanar.
Biyun da ‘yan mintuna su yasmine da aminata suka shigo da abincin rana. Muryoyinsu kadai suka sake haifarwa da zuciyarta wani sabon rudanin. Yanzun fa kenan itan ba daidai take dasu ba?,dukkansu sun fita walwala nutsuwar zuciya da kuma ‘yanci?,a cikinsun yanzun itace daban kenan?. Har suka gama leqata suka mata sannu bata motsa ba kaman yadda takewa kowa. Hankalin ama yana kai,don haka bibi na fita sallah ta sanya kowa yabar dakin,ta maida qofa ta rufe sannan ta tako a nutse inda sultanan ke kwance.
Kiran sunanta tayi amma bata amsa ba,bata tsaya batawa kanta lokaci ba ta durquso saman kanta ta kuma sanya hannayenta dukka biyun tana dagota daga kwanciyar tana fadin
“Haba sultanan bibi…..subhanallah” ama ta fadi kuma daga baya bayan taji yadda jikinta ya dumame da wani mugun zazzabi. Zagayowa tayi ta zauna sosai kusa da ita tana riqe tafin hannunta idanunta akan rufaffun idanuwanta
“Yanzun da wannan zazzabin a jikinki kike kwance?,sultana kinason kashe kanki ne?,kinaso yayi miki dariya yace yayi winning a kanki?,kinaso yaji cewa burinsa ya cika na cusguna miki?,kinason sanyawa bibi hawan jini ne?,ko kinaso aba ya shiga matsananciyar damuwar da zai dinga kasa komai?” Shuru bata amsa ba,saidai kukanta yanzun ya qaru ya zama me sauti ba kaman daxu da take yinsa silently ba. Tana jin inama ace ama zata iya farka qirjinta ta cire mata zuciyar daga qirjinta ko zata samu sassaucin abinda takeji,inama ace mutum yana iya shafe rayuwarsa gaba daya ya sake rubuta sabuwa,inama ace ta rufe ido ta bude taga ba itace sultanar familyn MAYAK’I ba
“Sultana…..babu ci babu sha babu shan magani,me kikeson yi idan ba kisan kai ba?,kina azabtar da kanki bayan shi wanda yayi miki laifin har yanzu bai waiwayi gida ba bare yasan kinayi,me yasa kike azabtar d kanki da kanki?,duba……yanzu lokacin sallah ne amma tunaninki ko kiyi sallar baya baki?” Sake barkewa tayi da kukan tana cusa fuskarta tsakanin cinyar ama tare da qanqame ama da kyau. Kuka takeyi sosai me sauti,sautin kukan dake fita da wani irin mugun radadi da ciwo da zukata suka tara. Sosai ta sake karya zuciyar ama,sai ta dora hannunta saman kanta tana shafa sassalkan gashinta da ya zama kamar na tsohuwar mahaukaciya tsakanin jiya da yau saboda tsananin firgici da tashin hankalin da take ciki. Sumar da ake bata lokaci wajen gyarata da qalqaleta amma a yau bata da maraba da radaddagaggen zare cikin tarin tarkacen bola. Ta yarda da maganar Dr chafa’atou sai anyi da gaske akan sultana din,idan ba haka ba depression din tsaf zaya kamata. Bata dakatar da ita daga kukan ba,saidai itama tata zuciyar tayi nisa wajen tunanin yadda zata tafi da yarinyar.
Sai da tayi shuru don kanta sannan ta dagata tana cewa
“Banaso daga yanzu ki sake irin haka sultana,idan maina ya tsaneki ya zalunceki ya kuma cusguna miki mu dukka nan ke mukeso,mu dukkaninmu walwala da farincikinki mukeso,kuma zaya dawo ya fuskanci mafi girman hukunci,hukuncin da kuma kece zaki zabeshi da kanki”. A duk sanda ta furta sunan Aliyyu ko maina sai taji wani abu tsakiyar kanta yana mata yawo kamar ana sakatar qwaqwalwarta,ambatar sunansa kadai yana sake sanya mata wata mahaukaciyar tsanarsa da takejin tamkar zuciyarta zata tsage ta fado,to amma batun hukuntashi dake hannunta kamar yadda ama ta furta sai ta samu kanta da laluben amsa,cikin manya manyan hukunce hukuncen da akema dan adam cikin rayuwa batasan wanne iri zata zaba masa ba,take kuma taji kanta ya sara kamar zai rabe biyu,tunaninsa ko daya bata qauna cikin kwanyarta,karon farko ta bude bakinta a hankali muryarta na fita da wani irin sarqaqqen amo
“Ama don Allah…..kibar kiramin sunanshi…..kaina kamar zai rabe biyu” ta qarasa maganar dukka jikinta yana kakkarwa saboda wani sabon zazzabi me cakude da ciwon kai daya sake saukar mata.
Yadda taga jikin nata yana rawa tilas ta kiranyi likita,a sannan dr chafa’atou ta fita sai dr nadra. Dr nadra tafi Dr chafa’atou fusata da lamarin,ta sake checking sultana da kyau tace a dakatar da shigowar masu dubiya,idaninta kuma da magariba likitan idanu Dr nouhou zai shigo zai dubata. A barta ta huta kawai,a qyaleta duk abinda take so tayin,shine zai sanya zuciyarta samun sassauci daga abinda takeji.
To ba’a sake matsa matan ba,saidai duka ranar ama din tana tsaye akan sultana din,sai yamma liqis ruwan da suka sanya mata ya qare,ama ta lallaba ta sanyata tayi alwala tayi sallah daga zaune saboda dinkin da yake jikinta,ta hilaceta da qyar ta samu tasha tea cokali uku,na hudun kuwa dawowa yayi bai iya shiga cikinta ba. Ganin hakan sai ta qyaleta,tana fatan gobe tasha abinda yafi hakan.
Suna tsaye daga bakin window inda zasu dinga hangota sosai ita da bibi din data gagara tafiya guda tun safen. Wayarta na hannunta dai still ya zuwa yanzu batasan adadin sau nawa tayi kiran layin maina ba. Duk sanda zata kira akace mata wayarsa na akashe sai taji ranta ya ninninka baci akan na baya. Me yaron yake nufi?,ya maishesu mutanen banza kenan?,yayi aika aikarsa ya wuce gararin gabansa babu abinda ya shalleshi?,baya tunanin a yanayin da ya barta ma ya dawo ya tabbatar da ingancin rayuwarta ko kuma akasin haka?.
Isowar likita gab da dakin ya sanyasu motsawa,yace a dauko wheelchair a kawota ya duba idanun nata. Numfashi ama ta sauke tana duban bibi,dukkansu a firgice suke,sannan kowannensu kana kallon fuskarsa zakaga yayi wata rama tsakanin jiya da yau kawai
“Bibi dare yana yi, inaga ya kamata ki wuce gida hakanan kodon yanayin jikinki,na miki alqawarin zan bawa sultana dukkan kulawa tamkar yadda mahaifiya zata bawa d’anta na cikinta kulawa”
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 12
Ko daya bibi bata da haufi da ama,kaf yaran gidan a gabanta aka haifesu,kuma babu wani wanda ya taba kuka da ita. Abu daya ne da ita,bata daukan raini ko qanqani,bata kuma son sakarci,duk wanda ya santa ya santa da wannan halin,don haka babu haufi bibi din tabar mata sultana,saidai kafin ta tafin tabar musu tanja saboda ama din kanta ta samu sauqin zirga zirga,sannan kuma tace da ama din
“Kome ake ciki banason ki boyemin,daga maina har sultana dukkansu jini na ne,kuma jikokina ne”
“In sha Allah bazan boye miki komai ba” ama ta furta tana lanqwasa yatsunta tana jin wani nauyi bibin ta sake aza mata.
Sun kusa a qalla awa biyu harda wani abu kafin Dr cha’aibou ya kammala gwaje gwajensa. Ya daga result na gwajin da aka yima idanun nan cikin asibitin yana kalla sai ya maida takardar saman teburinsa yana duban ama
“Ta samu matsalar rainin gani a idonta guda daya,jijiyoyin dake dauko haske sun tabu saboda duka da ya samesu ko buguwa…..” A firgice ta juya tana duban sultana saboda yadda sakamakon ya daketa da kyau. Idanunta fes ta zubewa sultanar,tana zaune saman lallausan kujerar da Dr din yace ta zauna akai,ko motsi kyakkyawa batayi ba bare wani reaction,itakam meye wai ya rage mata?,ita a yanzu ko cewa akayi maina ya kasheta dawowa tayi sam ba zatayi mamaki ba
“Amma ba damuwa in sha Allah,zamu dorata saman magani zuwa wani lokaci mu gani?,idan kuma akwai buqatar ayi mata glass zuwa lokacin zamu gani” ya fadi yana zaro takarda yayi rubuce rubuce akai.
Hawaye kawai idanun ama keson xubarwa amma tana dannewa,don ta tabbatar muddin ta zubda hawaye akan maina alhali yana raye ko a macen ma tamnar ruwan masifa ta fidda masa. Tsananin tausayin sultanar kamar ya fasa zuciyarta. Cikin qasa da awa ashirin da hudu duka yarinyar kamanninta sun jirkice,tayi wata irin wawuyar ramar da hatta rigunanta basa zaunar mata sosai a jikinta.
Da qyar da daren ta lallabata tasha madararta,madararta ta amana wadda muddin bata shata ba kaf gidan babu me rintsawa,amma sai gashi wai yau lallabata akeyi tasha din.
Kamar jiya bacci ya riga daukar sultana kafin ita,kaman jiyan dai haka ta zauna,gefe qur’ani gefe wayarta tana tusa kiran maina amma dai komai bai canza ba.
Batafi awa biyu da zama ba sultanan ta farka firgice tana kiran sunan maina din da qarfin. Da ita da tanja da itama ta fara bacci batasan waye ya riga wani isa gareta ba. Kuka take sosai dafe da kanta,ta ture hannuwan ama dake riqe da ita da qarfi,sai ama din ta fahimci kaman batason ganinta. Bataji komai ba don tasan situation din da take ciki,kuma Dr chafa’atou ta mata bayanin komai,zata iya tsintar kanta cikin razana da firgita da kuma miyagun mafarkai na abubuwan da suka faru da ita. Don haka ta yiwa tanja alama taja da baya ta basu waje.
Sun kusa kwashe wata awar tanja na lallabata da hikimomi da dabarun data saba mata kafin ta samu kukan yaja baya,ta bata ruwa tasha saita maida bayanta kawai ta kwanta hawayen na ratsa gashin idanunta yana jiqasu da hawayen dake diga har cikin kunnenta.
A wannan daren ma sam ama bata iya bacci ba,tunani ba kalar wanda batayi ba,a haka asuba ta rusketa.
****Kwanaki bakwai kenan da faruwar abun amma babu abinda ya canza. Al’amarin da ya haifar da rashin walwala rashin kuzari da karsashi cikin family din MAYAK’I. Kusan dukka sa’aninta dake gidan tamkar suma sun shiga alhini na abinda ya farun. Cikin dangi kuwa masu zuwa dubiya ne keta zarya,dadinta daya Dr chafa’atou ta hana shiga wajenta saboda tana buqatar hutu da qarancin hayaniya. Abinda ya daurewa ama kai shine fitar zancan, saidai bata da tabbacin sunsan ainihin abinda yayi silar kwanciyartata.
Daga ama har bibi babu wanda bai rame ba,kada ma ama taji labari wadda kullum dare tausayin sultana yake sanyata a gaba. Kowanne dare yarinyar cikin firgici da kuka take yinsa,idan an dace bacci ya dauketa kuma tun batayi nisa ba take farkawa a razane,muddin tayi wannan razanar kuma nata baccin ya qare itama.
Fargaba zullumi da rashin isashen bacci ga jinya suka taru suka yiwa ama din yawa. Gefe guda ga aba wanda bata sake ganin walwalarsa ba tun daga wancan ranar. Kullum rana zai shigo da safe ya duba sultana din,ya jima da ita yana tambayarta me takeso?,saidai babu um ba um um,hakan da dare zai sake dawowa ya kashe lokaci wajenta.
Rashin maganarta ya fara tabashi,tsahon zamanin da aka haifi sultana bata taba zaman minti.biyar bakinta shuru ba,koda bata da lafiya bata lamunci zaman kurum ba,abun ya soma ganin ya wuce tunaninsa,yadda takebin kowa da komau da idanu,tana iya yin kwanaki koda nawa ne a hakan ba tare da buqatar canjin yanayi ba, kodon haka a kwana na takwas ya sanya Dr chafa’atou a gaba yace lallai ayi mata gwaje gwaje ko bayan idanunta da ya kusa nakasa mata qila ya shaqe mata mafitar maganarta ma,don wanda yayi hakan babu abinda bazai aikata ba.
Dan dariya maganar ta bawa Dr chafa’atou,itadai tasan lafiya gurin yake,zallar daya daga cikin illolin da irin wadannan abubuwan suke haifarwa ne kawai data tsinci kanta a ciki. Don dai hankalinsa ya kwanta ta sanya akayi mata gwaje gwaje,kuma komai ya fito normal,ta bashi gwajin tana cewa
“Kulawa ta musamman kawai take buqata aci gaba da bata,don kamar depression ne take ciki har yanzu,komai zai wuce in sha Allah,a yawaita faranta mata ranta da dukkan abinda akasan tafiso,tare da qauracewa furtawa ko tuna duk abinda zai sakata a damuwa”. Lafiyar tata da aka tabbatar masa tayi masa dadi,sai ya qara adadin lokutan zuwansa,ya zauna yayita janta da irin hirarrakin da a baya yasan tafiso. Kafin wani lokaci dakin asibitin nata ya cika da kayayyaki,kama daga teddies chocolates,madararta,games kala kala da tarkacen kayan computer. Komai saidai ta bishi da ido,yadda zai gwada mata ya aje shi a wajen bata sake tabashi. Tana jin bata qaunar komai,bata buqatar komai,hakanan komai bai bata sha’awa,inda zasu gane su qyaleta ita daya cikin daki,kowa kada ya kulata,kowa kada ya tanka mata da hakan zaifi faranta mata. Don kusan kowa ta gani da ya danganci gidansu bata ganin komai tattare dashi sai ALIYYU MAINA,suna Mafi girman da ta yiwa mafifiyar tsana,sunan da inda tana da hali da daga rana irin ta yau ta shafeshi a doron duniya,halittar da takejin a rayuwa babu halittar data cancanci azaba irinta.
Sannu sannu komai bai canza ba illa ciwukan jikinta da suka warke din,kumburin fuskarta ya sabe dai dan tabbai masu launin pink,hakanan dinkin qasanta ma ya hade kasancewar akwai quruciya tattare da ita,sannan kuma ama ta tsaya tsayin daka tayi bata kyakkyawar kulawar da banda ciwon dake cikin zuciyarta da babu abinda zai hanata mulka qiba. To a maimakon qibar sai wata mummunar rama da tayi mara kyan gani.
Kwanansu ashirin cif Dr chafa’atou ta tabbatar da samun lafiyarta ta kuma rubuta mata sallama tare da bawa ama qarin shawarwarin yadda zata ci gaba da kulawa da ita don a samu rayuwarta ta koma daidai kamar ta kowa.
Motoci biyu ne cikin motocin gidan iyalin mayak’i sukazo daukarsu. Karon farko da ta fita daga asibitin tun ranar da ta kawo sultana. Tun dava randa ta koma ta wanke zanin gadonsu bata sake barin asibitin ba,don duk inda zata motsa sai taga kamar sultana zata rasa wata kulawar,kamar sultana zata buqaceta,kamar wani abun zai samu sultana din kafin ta dawo.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 11
“karka damu alhaji,in sha Allah zamuyi duka bakin qoqarinmu” kai kawai ya jinjina sannan ya waiwaya yana duban ama
“Na kirashi yafi sau shurin masaki ban sameshi ba,ban sani bama ko blocking dina yayi?,me yiwuwa tunda ke uwarsa ce bazai iya miki haka ba,idan kin sameshi ki shaida masa saqon da yabar mana ya riskemu,munga result kuma a qasa mun gode” daga wannan ya sanya kai ya fice,sai ama ta bishi da kallo baki sake. Me aba yake nufi ne?,baisan yadda suke nemansa itama hakan bane,ta kirayeshi bata sameshi ba?,sannan tayi zaton zaiyi maganar ya dawo gida ne ya karbi hukuncin da ya dace dashi,a maimakon hakan sai taji wata magana ma yakeyi daban wadda a nata ganin a yanzun ba nanata maganar bane ya kamata a dinga yi,abinda yafi kyau shine asan meye abu na gaba da ya kamata ace an aiwatar.
K’arfe bakwai da rabi sai ga bibi an kawota,ita da matar oncle umar. Jikinta sanye da lallausar bubu cotton ‘yar saudiyya,hannunta riqe da casbahar da kana gani kasan itama ita ta kwana ja. Dukkansu suna a gaban gadon sultanar suna mata sannu,saidai ba wanda ta tankawa,hasalima ko qwayar idanuntan taqi ta bude ta kalli koda bibi dinne,sai hawaye da suke bulbulowa ta qasan idanun. Juyin duniya bibi tayi ta bude ido amma ta qiya,duk da dama daya idon ba wani buduwa yakeyi sosai ba,koda ta bude dinma bawai ganin komai tarwai takeyi ba.
Da bibin ta gaji ta koma lallabata ta tashi taci abinci,abincin da tafiso ta sanya tanja ta dafa mata tun sassafe,shima har bibi din tayi ta gama bata ko motsa ba bare ta nuna tasan me sukeyi,daga qarshe ma sai ta gyara kwanciyarta ta basu baya ta fuskanci bango sanda ‘yan dubiya suka fara isowa dakin.
Ita daya tasan me takeji cikin zuciyarta,wani baqinciki da wani abu me tauri ne tokare tsakiyar maqoshinta. Kunyar kallon kowa takeji,hakanan kuma haushin kowa takeji. Ta tabbatar inda bibi bata biyewa umarninsa ba ta sakata a gaba sun tafi yadda suka saba da yanzun babu abinda ya sameta. Kusan ta tarkata dukka laifin ne ta azawa bibin,tana ganin sassaucin da ta yiwa maina dinne har ya samu qofar aiwatar da mummunar nufinsa a kanta.
Wasa wasa sai gashi takai har qarfe biyu na rana bataci komai ba,maganinta ma babu wanda tasha a ciki sai uban kuka data saka gaba. Duk wani motsin sultana din yana kan idanun ama,a yanzun tana sake jinta ne kamar saddi,tana ji kuma har cikin rai da zuciyarta nauyinta ce sultana,dolenta ce sultanar.
Biyun da ‘yan mintuna su yasmine da aminata suka shigo da abincin rana. Muryoyinsu kadai suka sake haifarwa da zuciyarta wani sabon rudanin. Yanzun fa kenan itan ba daidai take dasu ba?,dukkansu sun fita walwala nutsuwar zuciya da kuma ‘yanci?,a cikinsun yanzun itace daban kenan?. Har suka gama leqata suka mata sannu bata motsa ba kaman yadda takewa kowa. Hankalin ama yana kai,don haka bibi na fita sallah ta sanya kowa yabar dakin,ta maida qofa ta rufe sannan ta tako a nutse inda sultanan ke kwance.
Kiran sunanta tayi amma bata amsa ba,bata tsaya batawa kanta lokaci ba ta durquso saman kanta ta kuma sanya hannayenta dukka biyun tana dagota daga kwanciyar tana fadin
“Haba sultanan bibi…..subhanallah” ama ta fadi kuma daga baya bayan taji yadda jikinta ya dumame da wani mugun zazzabi. Zagayowa tayi ta zauna sosai kusa da ita tana riqe tafin hannunta idanunta akan rufaffun idanuwanta
“Yanzun da wannan zazzabin a jikinki kike kwance?,sultana kinason kashe kanki ne?,kinaso yayi miki dariya yace yayi winning a kanki?,kinaso yaji cewa burinsa ya cika na cusguna miki?,kinason sanyawa bibi hawan jini ne?,ko kinaso aba ya shiga matsananciyar damuwar da zai dinga kasa komai?” Shuru bata amsa ba,saidai kukanta yanzun ya qaru ya zama me sauti ba kaman daxu da take yinsa silently ba. Tana jin inama ace ama zata iya farka qirjinta ta cire mata zuciyar daga qirjinta ko zata samu sassaucin abinda takeji,inama ace mutum yana iya shafe rayuwarsa gaba daya ya sake rubuta sabuwa,inama ace ta rufe ido ta bude taga ba itace sultanar familyn MAYAK’I ba
“Sultana…..babu ci babu sha babu shan magani,me kikeson yi idan ba kisan kai ba?,kina azabtar da kanki bayan shi wanda yayi miki laifin har yanzu bai waiwayi gida ba bare yasan kinayi,me yasa kike azabtar d kanki da kanki?,duba……yanzu lokacin sallah ne amma tunaninki ko kiyi sallar baya baki?” Sake barkewa tayi da kukan tana cusa fuskarta tsakanin cinyar ama tare da qanqame ama da kyau. Kuka takeyi sosai me sauti,sautin kukan dake fita da wani irin mugun radadi da ciwo da zukata suka tara. Sosai ta sake karya zuciyar ama,sai ta dora hannunta saman kanta tana shafa sassalkan gashinta da ya zama kamar na tsohuwar mahaukaciya tsakanin jiya da yau saboda tsananin firgici da tashin hankalin da take ciki. Sumar da ake bata lokaci wajen gyarata da qalqaleta amma a yau bata da maraba da radaddagaggen zare cikin tarin tarkacen bola. Ta yarda da maganar Dr chafa’atou sai anyi da gaske akan sultana din,idan ba haka ba depression din tsaf zaya kamata. Bata dakatar da ita daga kukan ba,saidai itama tata zuciyar tayi nisa wajen tunanin yadda zata tafi da yarinyar.
Sai da tayi shuru don kanta sannan ta dagata tana cewa
“Banaso daga yanzu ki sake irin haka sultana,idan maina ya tsaneki ya zalunceki ya kuma cusguna miki mu dukka nan ke mukeso,mu dukkaninmu walwala da farincikinki mukeso,kuma zaya dawo ya fuskanci mafi girman hukunci,hukuncin da kuma kece zaki zabeshi da kanki”. A duk sanda ta furta sunan Aliyyu ko maina sai taji wani abu tsakiyar kanta yana mata yawo kamar ana sakatar qwaqwalwarta,ambatar sunansa kadai yana sake sanya mata wata mahaukaciyar tsanarsa da takejin tamkar zuciyarta zata tsage ta fado,to amma batun hukuntashi dake hannunta kamar yadda ama ta furta sai ta samu kanta da laluben amsa,cikin manya manyan hukunce hukuncen da akema dan adam cikin rayuwa batasan wanne iri zata zaba masa ba,take kuma taji kanta ya sara kamar zai rabe biyu,tunaninsa ko daya bata qauna cikin kwanyarta,karon farko ta bude bakinta a hankali muryarta na fita da wani irin sarqaqqen amo
“Ama don Allah…..kibar kiramin sunanshi…..kaina kamar zai rabe biyu” ta qarasa maganar dukka jikinta yana kakkarwa saboda wani sabon zazzabi me cakude da ciwon kai daya sake saukar mata.
Yadda taga jikin nata yana rawa tilas ta kiranyi likita,a sannan dr chafa’atou ta fita sai dr nadra. Dr nadra tafi Dr chafa’atou fusata da lamarin,ta sake checking sultana da kyau tace a dakatar da shigowar masu dubiya,idaninta kuma da magariba likitan idanu Dr nouhou zai shigo zai dubata. A barta ta huta kawai,a qyaleta duk abinda take so tayin,shine zai sanya zuciyarta samun sassauci daga abinda takeji.
To ba’a sake matsa matan ba,saidai duka ranar ama din tana tsaye akan sultana din,sai yamma liqis ruwan da suka sanya mata ya qare,ama ta lallaba ta sanyata tayi alwala tayi sallah daga zaune saboda dinkin da yake jikinta,ta hilaceta da qyar ta samu tasha tea cokali uku,na hudun kuwa dawowa yayi bai iya shiga cikinta ba. Ganin hakan sai ta qyaleta,tana fatan gobe tasha abinda yafi hakan.
Suna tsaye daga bakin window inda zasu dinga hangota sosai ita da bibi din data gagara tafiya guda tun safen. Wayarta na hannunta dai still ya zuwa yanzu batasan adadin sau nawa tayi kiran layin maina ba. Duk sanda zata kira akace mata wayarsa na akashe sai taji ranta ya ninninka baci akan na baya. Me yaron yake nufi?,ya maishesu mutanen banza kenan?,yayi aika aikarsa ya wuce gararin gabansa babu abinda ya shalleshi?,baya tunanin a yanayin da ya barta ma ya dawo ya tabbatar da ingancin rayuwarta ko kuma akasin haka?.
Isowar likita gab da dakin ya sanyasu motsawa,yace a dauko wheelchair a kawota ya duba idanun nata. Numfashi ama ta sauke tana duban bibi,dukkansu a firgice suke,sannan kowannensu kana kallon fuskarsa zakaga yayi wata rama tsakanin jiya da yau kawai
“Bibi dare yana yi, inaga ya kamata ki wuce gida hakanan kodon yanayin jikinki,na miki alqawarin zan bawa sultana dukkan kulawa tamkar yadda mahaifiya zata bawa d’anta na cikinta kulawa”
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 12
Ko daya bibi bata da haufi da ama,kaf yaran gidan a gabanta aka haifesu,kuma babu wani wanda ya taba kuka da ita. Abu daya ne da ita,bata daukan raini ko qanqani,bata kuma son sakarci,duk wanda ya santa ya santa da wannan halin,don haka babu haufi bibi din tabar mata sultana,saidai kafin ta tafin tabar musu tanja saboda ama din kanta ta samu sauqin zirga zirga,sannan kuma tace da ama din
“Kome ake ciki banason ki boyemin,daga maina har sultana dukkansu jini na ne,kuma jikokina ne”
“In sha Allah bazan boye miki komai ba” ama ta furta tana lanqwasa yatsunta tana jin wani nauyi bibin ta sake aza mata.
Sun kusa a qalla awa biyu harda wani abu kafin Dr cha’aibou ya kammala gwaje gwajensa. Ya daga result na gwajin da aka yima idanun nan cikin asibitin yana kalla sai ya maida takardar saman teburinsa yana duban ama
“Ta samu matsalar rainin gani a idonta guda daya,jijiyoyin dake dauko haske sun tabu saboda duka da ya samesu ko buguwa…..” A firgice ta juya tana duban sultana saboda yadda sakamakon ya daketa da kyau. Idanunta fes ta zubewa sultanar,tana zaune saman lallausan kujerar da Dr din yace ta zauna akai,ko motsi kyakkyawa batayi ba bare wani reaction,itakam meye wai ya rage mata?,ita a yanzu ko cewa akayi maina ya kasheta dawowa tayi sam ba zatayi mamaki ba
“Amma ba damuwa in sha Allah,zamu dorata saman magani zuwa wani lokaci mu gani?,idan kuma akwai buqatar ayi mata glass zuwa lokacin zamu gani” ya fadi yana zaro takarda yayi rubuce rubuce akai.
Hawaye kawai idanun ama keson xubarwa amma tana dannewa,don ta tabbatar muddin ta zubda hawaye akan maina alhali yana raye ko a macen ma tamnar ruwan masifa ta fidda masa. Tsananin tausayin sultanar kamar ya fasa zuciyarta. Cikin qasa da awa ashirin da hudu duka yarinyar kamanninta sun jirkice,tayi wata irin wawuyar ramar da hatta rigunanta basa zaunar mata sosai a jikinta.
Da qyar da daren ta lallabata tasha madararta,madararta ta amana wadda muddin bata shata ba kaf gidan babu me rintsawa,amma sai gashi wai yau lallabata akeyi tasha din.
Kamar jiya bacci ya riga daukar sultana kafin ita,kaman jiyan dai haka ta zauna,gefe qur’ani gefe wayarta tana tusa kiran maina amma dai komai bai canza ba.
Batafi awa biyu da zama ba sultanan ta farka firgice tana kiran sunan maina din da qarfin. Da ita da tanja da itama ta fara bacci batasan waye ya riga wani isa gareta ba. Kuka take sosai dafe da kanta,ta ture hannuwan ama dake riqe da ita da qarfi,sai ama din ta fahimci kaman batason ganinta. Bataji komai ba don tasan situation din da take ciki,kuma Dr chafa’atou ta mata bayanin komai,zata iya tsintar kanta cikin razana da firgita da kuma miyagun mafarkai na abubuwan da suka faru da ita. Don haka ta yiwa tanja alama taja da baya ta basu waje.
Sun kusa kwashe wata awar tanja na lallabata da hikimomi da dabarun data saba mata kafin ta samu kukan yaja baya,ta bata ruwa tasha saita maida bayanta kawai ta kwanta hawayen na ratsa gashin idanunta yana jiqasu da hawayen dake diga har cikin kunnenta.
A wannan daren ma sam ama bata iya bacci ba,tunani ba kalar wanda batayi ba,a haka asuba ta rusketa.
****Kwanaki bakwai kenan da faruwar abun amma babu abinda ya canza. Al’amarin da ya haifar da rashin walwala rashin kuzari da karsashi cikin family din MAYAK’I. Kusan dukka sa’aninta dake gidan tamkar suma sun shiga alhini na abinda ya farun. Cikin dangi kuwa masu zuwa dubiya ne keta zarya,dadinta daya Dr chafa’atou ta hana shiga wajenta saboda tana buqatar hutu da qarancin hayaniya. Abinda ya daurewa ama kai shine fitar zancan, saidai bata da tabbacin sunsan ainihin abinda yayi silar kwanciyartata.
Daga ama har bibi babu wanda bai rame ba,kada ma ama taji labari wadda kullum dare tausayin sultana yake sanyata a gaba. Kowanne dare yarinyar cikin firgici da kuka take yinsa,idan an dace bacci ya dauketa kuma tun batayi nisa ba take farkawa a razane,muddin tayi wannan razanar kuma nata baccin ya qare itama.
Fargaba zullumi da rashin isashen bacci ga jinya suka taru suka yiwa ama din yawa. Gefe guda ga aba wanda bata sake ganin walwalarsa ba tun daga wancan ranar. Kullum rana zai shigo da safe ya duba sultana din,ya jima da ita yana tambayarta me takeso?,saidai babu um ba um um,hakan da dare zai sake dawowa ya kashe lokaci wajenta.
Rashin maganarta ya fara tabashi,tsahon zamanin da aka haifi sultana bata taba zaman minti.biyar bakinta shuru ba,koda bata da lafiya bata lamunci zaman kurum ba,abun ya soma ganin ya wuce tunaninsa,yadda takebin kowa da komau da idanu,tana iya yin kwanaki koda nawa ne a hakan ba tare da buqatar canjin yanayi ba, kodon haka a kwana na takwas ya sanya Dr chafa’atou a gaba yace lallai ayi mata gwaje gwaje ko bayan idanunta da ya kusa nakasa mata qila ya shaqe mata mafitar maganarta ma,don wanda yayi hakan babu abinda bazai aikata ba.
Dan dariya maganar ta bawa Dr chafa’atou,itadai tasan lafiya gurin yake,zallar daya daga cikin illolin da irin wadannan abubuwan suke haifarwa ne kawai data tsinci kanta a ciki. Don dai hankalinsa ya kwanta ta sanya akayi mata gwaje gwaje,kuma komai ya fito normal,ta bashi gwajin tana cewa
“Kulawa ta musamman kawai take buqata aci gaba da bata,don kamar depression ne take ciki har yanzu,komai zai wuce in sha Allah,a yawaita faranta mata ranta da dukkan abinda akasan tafiso,tare da qauracewa furtawa ko tuna duk abinda zai sakata a damuwa”. Lafiyar tata da aka tabbatar masa tayi masa dadi,sai ya qara adadin lokutan zuwansa,ya zauna yayita janta da irin hirarrakin da a baya yasan tafiso. Kafin wani lokaci dakin asibitin nata ya cika da kayayyaki,kama daga teddies chocolates,madararta,games kala kala da tarkacen kayan computer. Komai saidai ta bishi da ido,yadda zai gwada mata ya aje shi a wajen bata sake tabashi. Tana jin bata qaunar komai,bata buqatar komai,hakanan komai bai bata sha’awa,inda zasu gane su qyaleta ita daya cikin daki,kowa kada ya kulata,kowa kada ya tanka mata da hakan zaifi faranta mata. Don kusan kowa ta gani da ya danganci gidansu bata ganin komai tattare dashi sai ALIYYU MAINA,suna Mafi girman da ta yiwa mafifiyar tsana,sunan da inda tana da hali da daga rana irin ta yau ta shafeshi a doron duniya,halittar da takejin a rayuwa babu halittar data cancanci azaba irinta.
Sannu sannu komai bai canza ba illa ciwukan jikinta da suka warke din,kumburin fuskarta ya sabe dai dan tabbai masu launin pink,hakanan dinkin qasanta ma ya hade kasancewar akwai quruciya tattare da ita,sannan kuma ama ta tsaya tsayin daka tayi bata kyakkyawar kulawar da banda ciwon dake cikin zuciyarta da babu abinda zai hanata mulka qiba. To a maimakon qibar sai wata mummunar rama da tayi mara kyan gani.
Kwanansu ashirin cif Dr chafa’atou ta tabbatar da samun lafiyarta ta kuma rubuta mata sallama tare da bawa ama qarin shawarwarin yadda zata ci gaba da kulawa da ita don a samu rayuwarta ta koma daidai kamar ta kowa.
Motoci biyu ne cikin motocin gidan iyalin mayak’i sukazo daukarsu. Karon farko da ta fita daga asibitin tun ranar da ta kawo sultana. Tun dava randa ta koma ta wanke zanin gadonsu bata sake barin asibitin ba,don duk inda zata motsa sai taga kamar sultana zata rasa wata kulawar,kamar sultana zata buqaceta,kamar wani abun zai samu sultana din kafin ta dawo.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 13
Cikin jikin ama din take kwance luf,ga duk wanda yasan sultanan zai iya rantsuwa a yanzun ba ainihin sultana da ya sani bane,ta koma wata maras kuzari ko kadan,so silent,tana daukan lokaci me tsaho kafin ka tsinci kalma guda daga bakinta.
Bibi batasan da dawowarsu ba sai da suka isa farfajiyar gidan. Dukkan ma’aikata dake da duty da safen suka marmatso suna musu barka da zuwa tare da sakeyi mata sannu da jiki. Sannu da jikin da takejin kamar da gayya akeyi mata ita,duk wanda yace mata ya jiki maimakon taji dadin hakan sai wani bacin rai ya lullube.
Ama na fiddota bibi ta qaraso,ta sanya hannu ta taya ama fiddo ta
“Ki kwashe duka kayan ki shiga dasu ciki,wadanda keda buqatar gyara kuma a gyarasu don Allah” ama ta waiwaya tana riqe da sultana ta yima tanja umarni
“An gama ranki ya dade” ta fadi a ladabce sannan ta zagaya bayan motar tana yiwa modu driver maganar ya buda boot din.
“Sannu” bibi ta fada wadda ke riqe da hannun sultana daya. Kai kawai ta gyada mata bata iya kallon qwayar idanunta ba.
Sun taka har veranda din bibi da zata sadaka da ainihin qawataccen falon dattijuwar. Taku daya tak sultanan zatayi ta sanya qafafunta cikin falon,har ta daga qafar sai kuma ta maida ta sauke tana ja baya kadan tamkar wadda ta hangi wani shamaki a gabanta.
Daga bibin har ama duban fuskarta sukeyi,fuskar data sauya lokaci daya tana fidda wasu irin emotions dake nuna zurfin abinda ke danqare a zuciya
“Mu qarasa ciki sultana” bibi ta fadi tana dubanta. Sake girgiza kai tayi a karo na biyu,sai kuma ta juya da hanzari da qaramar sassarfa,tafiyar da tana yinta ne kawai amma iska ke barazanar bugar da ita daga hagu zuwa dama,sai ama ta take mata baya,sannan cikin hanzari ta sha gabanta gudun kada ta isa farfajiyar gidan kuma wani abun ya faru ta tara musu ‘yan kallo.
Koda tasha gabanta kuka take haiqan qirjinta na dagawa,zaka tsammaci gasar tseren gudu ta shiga. Kamo hannunta ama tayi da kyau ta damqe cikin nata hannun,bata manta da bitar da Dr chafa’atou tayi mata kafin barowarsu asibitin,don haka cikin tausasawa ta tambayeta
“Ki kwantar da hankalinki ki nutsu,u r safe,maina bai isa ya miki komai ba,yanzu ke ‘yar gatan bibi da ama ce,ga aba oncle omar oncle bashar ma” kai take jijjigawa,sannan cikin muryar kuka tace
“Bazan shiga ba ama”
“…..akwai abubuwan da zasu iya kada hankalinta su kuma firgitata,kamar wajen da abun ya faru,abubuwan dake zagaye da ita sanda komai ya faru da sauransu,so ayi qoqarin goge da kauda komai don kwanyarta ta samu cikakken waraka…..” Ama ta tuna maganganun Dr chafa’atou.
Ajiyar zuciya ta sauke tana jinjina kai
“Is okay ya isa,muje sashena,zaki zauna a dakina?” Idonta ta runtse hawayen dake maqale ya qarasa gangarowa,saita daga kanta a hankali tana ayyana ashe akwai ranar da zata guji rayuwar kusa da bibinta?,bibinta abar qaunarta?,ashe akwai sanda zataji gwara rayuwa nesa bibi?.
Batayi yunqurin maidata sassan bibi ba ta wuce da ita kai tsaye nata sashen,saidai bibin na biye dasu,don tana kai sultana dakinnata ta barta da daya daga cikin masu aikinta,ta kuma dawo falon don ta sanya a kwaso sauran kayanta dake dakinta can sassan bibi saiga bibi din da kanta.
“Wani abunne kuma hamdiyya?” Yadda bibi tayi tambayar a sanyaye sai tausayinsu su dukka ya kamata,a yau maina ya zama silar nesantarsu da juna duk da irin son da sukewa juna
“Ba komai bibi,zauna na miki bayani” a nutse ta fahimtar da bibin,ta kuma fahimta duk da fuskarta ya nuna lamarin bataso ya kasance haka ba,amma a yanzun samun cikakkiyar lafiyar sultanan da dawowarta hayyacinta shine gaba da komai.
Kafin yammaci komai na sultana ya koma sassan ama,ta fidda komai nata daga dakin ta sanya an sauya mata daki,ta barwa sultana wannan. Zuwa magariba komai ya kammala.
Da kanta bayan ta kintsa ta dawo ta saka sultana a gaba tayi wanka,ta bata kaya ta sauya sannan ta sake tusata sai data ci abinci. Abinci ne lafiyayye da tasan zai sanyata ta ciko ta kuma tada komada. Tana da buri da fatan nan da sati daya kacal ma sultana din ta sauya ta fara komawa sultananta ta asali.
Ko na minti daya ama bata barinta ita daya bare tayi wani tunani da zai hatsinata. Bayan sallar isha’i ta sanya bilki ta fiddota ta zauna falo kaman kowa.
Dai dai lokacin aman tana zaune saman daya daga cikin kujerun falon. Tab ce a hannunta tana duba hotunan kayayyakin dake cikin container dinta data sauka wadda bata samu nutsuwar dubawar ba sai yanzu,saidai rabin hankalinta na ga wayoyinta wai ko zataga gilmawar wani abu da ya shafi maina. Ita kanta ama din ta fada tayi fayau,amma wannan kyan dai da gayun nata yana nan. Ko a yanzun wani cotton material ne a jikinta da aka yiwa budadden dinki,dogon hannu ne saidai an tsagashi ta sama har kusa da damtsenta. Qafafunta na harde guri guda,saddi yana zaune daga qasa kusa da qafafun na yana tattare mata wasu takardu. Tunda taji alamun tahowar bilki ta shinfidadden marbles din dake malale a dukka ilahirin sassan ta dauke hankalinta daga tab din ta maida inda suke nufowar don taga sultanan tayi wankan kwanciya ta kuma sauya kayan kamar yadda tace mata tayi.
Batakai ga lura da wannan ba idanunta suka sauka kan fuskar sultanan,wadda gaba daya manyan fararen idanunta ke kafe waje daya a falon,sai kuma a hankali a hankali ta soma tsaiwa kafin taja da baya da gudu kuma ta koma ciki da sassarfa kuka yana qwace mata.
Kwata kwata ama batasan da shigowar aba ba sai data waiwaya tana duban abinda ya sanya sultanar razana da kuma komawa cikin. Babban hoton maina ne. Sanye da wasu kaya na asalin buzaye, kayansu na gargajiya,kanshi yasha nadin rawani irin nasu fari qal,kamar yadda ainihin kayan suke baqaqe ne da adon farin zare.
Hoto ne da ama din ke masifar so,saboda ya fita aininun,ya kuma fidda kamannin maina da baiwar zallar kyau da Allah yayi masa,kyawun dake cakude da quruciya da tashen shekaru.
“Kai saddi!,zo ka cire hotonnan” aba ya furta cikin kakkausar murya wani abu me zafi yana gilmawa ta cikin idanunsa. Ba musu saddi din ya miqe cikin sanyin jiki bayan ya ajema ama takardunta,ya nufi hoton yana jawo wani stool me kyau dake gefe wanda aka azama decoration flower,ya sauke flower din ya taka saboda tsahonsa bazai kai ba,maina dinne da kansa ya kafa hoton bayan an wankoshi,naira dubu talatin da biyar ama din ta bayar akayi mata shi.
Qasa ya saukeshi kamar yadda aba ya buqata,yana tsaye daga bayan saddi din ya sake cewa
“Juyashi ya kalli bango” juyashin yayi kamar yadda ya buqata,sai ya sake kallonsa
“Duk wani hoton aliyyu dake sassannan komai qanqatarsa a fiddashi,banaso na sake gani” ya fadi yana nuna saddi da yatsa kamar shine me laifin
“To aba” ya amsa masa cikin ladabi. Bai sake cewa komai ba ya juya yana wucewa qofar da zata sadashi da gefansa,sai sannan ama tayi qarfin halin cewa
“Sannu da zuwa”
“Yauwa” ya bata amsa yana dan dubanta kadan kafin yaci gaba da tafiya.
Rasa waye zatabi tayi cikin aba da kuma sultana?,daga qarshe ta yanke shawarar bin sultana din,don a yanzun ita keda cikakken buqatar a rarrasheta,aba kam batasan meke yawo a kansa ba,alamu sun nuna kamar ma dai ita yakewa kallon maina. Kallon saddi tayi daketa aikin bi yana kauda hotunan maina din, fuskarsa shima ta nuna yadda zuciyarsa ke masa rashin dadi,sai kawai ta fasa maganar ta juya tana fita a falon.
A takure ta sameta,fuskarta tsakiyar qafafunta tana rusgar kuka,wannan karon harda marayan sauti dake fita daga muryartata. Duk sanda taga kuka ya barke mata irin hakan tana narka zuciyar ama,tasan cewa yau koda da wayonta maina yayi mata haka dole taji abun har zuciyarta,koda tana sonshi,balle ita din da ta tabbatar babu komai tsakaninta da maina din sai ADAWA DA GABA DA KUMA TAKUN SAQA.
Qarfe goma harda rabi tabar dakin bayan bacci ya dauketa bayan ta gama koke kokenta. Ta fahimci bawai hotunan maina ba kawai,hatta da sunansa bata qaunar jin wani ya furta koda bawai ana nufin shi aliyyun ba.
Tanason shiga ta iske aba,amma sai zuciyarta tafi karkata da ta tafi dakin maina din.
Iya qurar dake jikin handle din qofar dakinsa kadai ta isheka amsar cewa yayi nisa da wajen,nisan da ko qofar dakin da alama babu wanda ya sake tabawa bare a samu sassaucin qurar dake sauka.
Ga mamakinta key din dakin yana maqale a jiki. Hannu tasa ta murza ta tura qofar ta shiga. Da idanu tabi falon nasa da kallo,falon da baya rabo da tsafta,falon da baya rabo da qamshi,falon da ko yaushe cikin qyale qyale yake,amma a yanzun qura ta soma samun wajen zama.
Takawa tayi cikin falon ta danyi shawagi,idanunta manne da hotunansa qwaya hudu rak dake maqale a bangon falon. Dauke kanta tayi ta tura qofar dakin gadon nasa wadda itama dai a bude take,barin qofar kuma a bude na sake haifar mata da tunani da kuma kokwanto me yawa.
Dan razana tayi kadan da ganin mutum cikin dakin,amma yana dago fuskarta data fahimci waye saita daidaita nutsuwarta
“Qaraso ciki mana” aba ya fada ganin taja ta tsaya daga qofa yana maida hankalinsa ga gurin da maina ke ajjiye duk wani abu nasa me muhimmanci
“Kema sahunshi kika biyo?” Ya sake jefawa ama tambayar. Ganin yanayin aba din kawai sai ya haifar mata da rauni
“Aba,kwana……..”
“Kwana goma sha hudu kenan ba…..babu shi ba dalilinsa,bai nememu ba bai kuma dawo gida ba,ai dama bazai dawo din ba,saboda mu din ba wasu mutane bane dake da muhimmanci a tattare dashi ba,inda muna da muhimmanci muna da kima da martaba tun asali da bai aikata abinda ya aikata din ba,yarinya qarama tsakiyar iyayenta da kakanninta, bashi da asara kota sisin kwabo shi yasa ya tsallaketa ya kuma biyo ya dakinsa ya iya tsaiwa tattara komai nasa me muhimmanci,kinga yabar mana saqo tare da tabbacin cewa kada muce zamu nemeshi,don a yanzun ya zama d’an kanshi bashi kuma da buqatar wasu iyaye”.
Kalaman aba daya bayan daya suka dinga dukanta har sai da suka sanyata sulalewa ta zauna gefen gadon maina dake a mulmule sai ‘yar qura data sauka akai. Hannunta har dan rawa yakeyi sanda ta kalli wajen taga kaf komai nashi da suka sani me daraja yana adanawa a wajen fes babu komai wajen. Duk da taga zahiri amma zuciyarta taqi aminta da nata zargin da kuma sharhin aba,sai ta fara girgiza kai idanunta suna nuna zallar tashin hankalin dake yawo a jiki da zuciyarta.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 14
Assalamualaikum warahmatullah*
“kar kayi haka aba,kaifa uba ne…. kada ka yanke hukunci cikin bacin rai da kuma zato…..”
“Wanne zato kike magana akai hamdiyya?,bayan ga zahiri?,ga zahirin da duk me hankali yasan inda ya dosa?,ya kuma san abinda yake nufi?”
“Aba…..don Allah ka tsaya mu tattauna…..bai kamat……”
“Meye bai kamata ba?,shin kinsan mummunar illar dake tattare da barin hawaye yana zuba a idanun maraya?,kinsan illar kukan maraya?” Kai ta girgiza da sauri
“To ya isheni hakanan,aliyyu yayi abinda rai da shaidan ya raya masa ko?,to nima banga abinda zai hanani daukan mataki a kansa ba”.
Ta sanshi farin sani,ta sanshi magana daya yake,ta kuma sanshi cewa kaifi daya ne,tunda yahau dokin naqi bazai saurareta ba,to amma ita din cikin jikimta da zuciyarta taqi gamsuwa da hasashen aba akan maina,bawai don tana daure masa qarqashi bane,a'ah......ita kanta taci alwashin hukuntashi a duk sanda ya bayyana cikin gidan,to amma kuma wannan shirun fa?,ba kwana daya ba biyu ba?,ba sati daya ba ba biyu ba?,shi din ba gwanin yin nesa da gida bane,hakanan ba gwanin son yawace yawace ba. Baya shan komai bashi kuma da abokan banza,ina yayi da nesa haka?.
Ita daya cikin dakin nasa bayan aba ya fice ya bata guri takewa kanta wadannan tambayoyin. Sai kawai ta fidda wayarta ta soma laluben numbers din mutum biyu cikin abokansa kuma roommate dinsa,wato faisal mus'ab.
Suna gama gaisawa suka cillo qorafin daukewar maina daga makaranta,bayan ya sani lokacine da suke dab da fara jarrabawa,ana da buqatarsa,jarabawa ce me matuqar muhimmanci wadda zata bashi damar shiga gaba ta biyu ta karatunsa,gabar kuma da zata baka tabbacin sake samun gurbi da kuma gindin zama cikin karatun.
Jikinta a sanyaye sukayi sallama dasu suma suna jimanta batun,wai ba'a san ina maina ya shiga ba?,kamar qaramin yaro?,hankalinsu yadan dagu saboda basusan ainihin abinda yake faruwa ba,sundai yima ana alqawarin bincikoshi muddin yana niamy cikin makaranta ko wajen makaranta.
Ji tayi kaman ta sanya hannunta saman kanta tayi kuka. Jarabawar da zasuyin yanzun ya jima yana bata labarinta tare da buqatar addu'arta. Ta tabbatar bawai qanqanin abu bane zai sanyashi tafiya ya barta ba,amma kuma tana saka ran ko ina ya shiga jarabawar dake tsaye a ranshi zata koro musu shi.
Da daya da daya take kiran duk wanda tasan zata iya samun wani abu game da maina,saidai har ta gama kiran aqalla mutum ashirin cif ba wanda yaga koda gittawarsa. Dole ta sare ta kuma tabbatar zaiyi wuya idan ba wata GAGARUMAR K'ADDARAR bace ke shirin sake tunkarota.
“où est-il allé?(ina ya tafi?)” Ta yiwa kanta da kanta tambayar da itama amsarta take nema.
****K’arfe sha daya ne na safiyar ranar asabar wadda ke dauke da yanayi maras zafi duk da cikin yanayin zafin ake. Saidai a ranar sosai zafin ya sassauta saboda alamu dake bayyana yiwuwar samun ruwan sama kowanne lokaci. Cikin gidanma babu wata hayaniya,don kusan duka yaran gidan sun fita da safen saboda yin siyayyar komawa makaranta a ranar litinin dinnan me zuwa.
Cikin qawataccen falon ama din wanda ke dada qara nuna alfarmarta da alfarmar dawwamar arziqin masu gidan,tamkar ma basu taba wani zamani da kalmar babu ta ratsa ta tsakaninsu ba. Sultana ce zaune saman daya daga cikin royal chairs na dinning din.
Cikin wata irin nutsuwa take zaunen,tana sanye da wasu cotton kaya hot pink. Gown ce me gajeran hannu data saukar mata har gwiwa,sai wandonta da ya lafe a jikinta. Kanta off_white silk scarf ne da ya lullube asirin sassalkan gashinta wanda ke daure a siririn band, yafi qarfin boyuwa ta cikin scarf din don haka ya fiddo ta qasansa ya bazu zuwa sassan kafadunta.
Warwaraye ne sirara guda hudu da ama ta siya mata a nigeria masu kyau masu kalan gold jere a kyakkyawan hannunta,ta sanya yatsanta guda daya tana wasa dasu ta hanyar warasu da kuma hadesu waje daya.
Tun daga qofan kitchen da ama ke takowa dauke da kofin madara take qare mata kallo. Cikin wata biyu da faruwar abun qaramin fadi tashi tayi ba wajen ganin sultana din ta farfado. Ciki kuwa harda dauketa da tayi sukabar nijer gaba daya suka tafi nigeria. A nigeria dukka tayi wasu yaqin,ta kuma samu nasarar don sultana din ta soma komawa hayyacinta. Burbushin damuwa da suka ragewa zuciyarta kusan dukka ta ciresu,ta karbi zaman Nigeria da kyau,ta canza sosai,abinda ya yiwa kusan kowa dadi. Duka duka basufi sati guda da dawowa ba.
Yanayin zaman da sultanan tayi saman kujera ya tabbatarwa ama wani tunanin takeyi. Abinda kuma sam bataso kenan,amma dan adam ne,duk yadda takai ga qurewa wajen ganin ta bata kulawa dole akwai abubuwan da bata isa ta hanata ba,dadin da takeji cikin ranta kawai shine sauyi da take sake samu,ta soma yin wani irin fresh,haskenta tamkar ana qara mata shi,qiba ce har yanzun babu ita sam.
“Tunanin me akeyi?,a bawa ama labari” ama ta fadi sanda ta isa gabanta tana jan kujera guda daya dake kusa da sultana din tana zama.
Dago fuskarta tayi suka hada idanu,sai sultana din ta dan saki murmushi,alamun kunya dukka suna nunawa cikin qwayar idanunta. Zata iya cewa ba zata iya tuna zaqi ko dandanon soyayyar uwa ba,amma adan tsukin da tsautsayin ya saukar mata ta samu dukkan wata kulawa da d'a ke samu wajen uwa. Wani irin sabo me tarin yawa ya shiga tsakaninta da ama irin wanda bai taba hadasu ba,har wasu lokutan idan ta kebe take mamakin ashe dama haka take da kirki?,ashe da gaske ne abinda su aminata ke fadi a kanta a baya?.
“Ba komai” ta fada da wani irin sanyi wanda ya soma zame mata dabi’a,sanyin da abaya sam sam sultana bata sanshi ba cikin rayuwarta.
“To Allah yasa,maza ungo” aman ta fada tana miqa mata mug din hannunta me dauke da madarar shanu data tafasa mata ita da duminta.
Bata musa ba ta miqa hannu ta dauka,a nutse takai bakinta sai kuma ta sauke tana duban cup din
“Yaya dai?” Ama data dauki wayarta tana son duba calendar don ganin yau din adadin kwanaki nawa maina ya qara rabonshi dasu ta furta tana kallon fuskar sultana
“Na qoshi” ta fadi a sanyaye tana dan dora hannunta saman wuyanta. Da mamaki ta dubeta
“Amma kaman ke kika cewa bilki a kawo zaki sha ko?” Kai kawai ta dagawa ama,sai ama din ta sake maida hankalinta kanta,cikin sassauta murya tace
“Sultana banaso ki dawo da dabi’ar qin cin abinci fa,don Allah karki maido mu baya kinji?,na lura tunda muka dawo nijer kike gujewa abinci,idan nijer dinne bakiso mu koma nigeria ne gaba daya to” kai ta girgiza mata alamun a’ah,sai kuna wasu siraran qwalla suka biyo fatar idanunta. Ita batasan yadda zata yiwa ama din bayani ba,kwata kwata kamar an cire mata sha’awar abinci,tanason ci amma da ta kaishi bakinta sai taji gaba daya ta qoshi,idan kuma ta tilastawa kanta din dai amai ya fara taso mata.
Ama ta lura da hawayen,hankalinta yadan dagu ta ajiye wayar tata saman table
“Idan kina da damuwa ni mamarki ce ki gayamin sultana” ta fadi mata tana ritsata da idanu.
“Ba komai,kawai qoshi nayi” ta bata amsa tana saka yatsunta tana dauke hawayen
“Ko madararki za’a kawo miki?,yanzun sai nayi waya niamy su sakota a jirgi don tafi saurin zuwa?” Kai ta sake girgiza mata alamun dai a’ah. Duk yadda ta rayu da qaunar madarar da shauqinta da kuma jin gardinta gaba daya yanzun bata burgeta
“Zansha wannan din anjima”
“Kinyi alqawari?”
“Eh” ta amsa mata,sai ama ta gyada kai sannan ta maida dubanta ga calendar din.
Lissafinta dai dai yake,kwanakin shurawa suke tamkar cikin mafarki,duk yadda take tunanin zuwa lokacin zai nemesu zai waiwayi gida zai dawo zai kirata koda a waya ne abun ya sabawa tunaninta,babu ko daya a ciki. Tayi cigiya iyakar yinta,har a kafafen tv da radio amma shuru kakeji. Aba kuma ya nade hannunsa yana kallonta,baice komai ba bai kuma sanya baki ba. Koda yaje Nigeria ma acan din su yaaya abdulhakeem fada suka dinga zabgawa kaman su ari baki
“Kuna wasa ne,dan mutum guda kamar batan nama a miya?” Sun kira aba amma har suka gama fadansu baice komai ba,daga qarshe yace dasu
“Aiba yaro bane qarami,ya fimu sanin ciwon kansa ma yanzun,duk inda yaje zai dawo tunda dai ba qanqanin jariri bane” ran uncle abdulhakeem ya baci qwarai,saboda ya fahimci kamar m abun bai dameshi ba. Hayatudden ne ya karba da yake ya fishi sanyi da sauqin kai yayi masa magana shima
“Kuma iyayensa ne,na baku wuqa da nama yaaya,kada ku damu” jin ya fadi hakan sai ya rabu dashi kawai. Cigiyar suma suka baza sosai,amma har suka gama zamansu suka dawo da nijer din da Nigerian ba wani bayani.
Tana shiga fargaba wasu lokutan,tana shiga tunani me zurfi kan yana ina,wanne hannu zai fada?,da waye zai hadu?,sai ta furzar da iska me zafi daga bakinta daidai sanda suka hada ido da sultana. Maida wayar tayi ta ajjiye cikin zuciyarta tana maimaita addu'ar data zama sirri tsakaninta da ubangijinta na ya bawa aliyyun tarbiyyarsa dama lafiyarsa kariya,kada ubangiji ya kamashi ko ya jarabcesu silar zubar hawaye a idanunsu.
“Meye ra’ayinki kan komawa makaranta?” Tayi maganar tana monitoring mode dinta. Ambatar makarantar kadai kuwa ya canza yanayinta din,tayi qas da kanta,saidai kafin tace komai sai ga yasmine ta shigo,rungume da ledar data tabbatar siyayyyar da suka fita yine
“Sultana ga mariam inoussa ita da aicha ousmane,muna dawowa muka gansu wai basusan a nan guraren kike ba,’yan uwan gidansu alhaji saddam ne ashe”. Kaf walwala da fara’ar fuskarta ta dauke,ta saki baki kawai tana duban yasmine kafin tayi magana a hankali
“Ki dakatar dasu ki gaya musu bacci nakeyi” ta fadi maganar da iyakacin gaskiyarta ne,saboda a yanzun bata qaunar hulda da duk wadanda ta sani a baya,musamman qawayenta na makaranta dama na cikin unguwa gaba daya. Gani takeyi kowa ma yasan meye ya faru da ita?,kuma kowa kallonta yakeyi da abun.
Turus yasime tayi tana duban sultana,kwata kwata ta canza,ko su dinma ba komai take shiga nasu ko ta sanya baki ba
“Yasmine,jeki ki gaya musun” ama ta yiwa yasmine magana,sai ta amsa tana juyawa tare da barin falon.
Tun a nan ta fahimci tana da buqatar canjin makaranta ne,don haka a washegari lahadi tayi mata register da wata makarantar daban. Makaranta ce me mugun tsada wadda har tafi waccan tata ta bayan tsada kuma tsari. Tasan muddin idan ba hakan tayi ba ba zata sake ba,gwara ta kaita cikin wadanda bata taba sani ba,yadda ba zatayi dari dari ko ta kasa sakewa tayi karatu cikinsu ba.
Duka a ranar lahadin ta sauya mata komai da komai,hatta da ruwa da drinks na zuwa makaranta da zata iya buqata kamar wata ‘yar free nursery.
Duk dai a ranar ta fidda mota guda cikin motocinta duk da dama already sultanan akwai motar kaita makarantar,amma tace a ajjiyeta,saboda tana da burin ta sake sabuwar rayuwa,batason komai nata data taba amfani dashi a baya yanzun a dawo dashi,don hatta da sutturu duk uban tulin kayan sawarta ta sanya tanja ta fiddasu,batasan rabawa sukayi tsakanin ma’aikatan ba ko menene oho,itadai duka tayi mata juyen closet nata.
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 15
les jumeaux(the twins)???
K'arfe biyu da rabi motocin yaran gidan dake jigilar kaisu makaranta suka fara saukesu,a lokacin ama tana zaune a samanta,tana jin motsi da kai kawonsu,saidai aikin da takeyi ya dauke mata hankali,batajin zata iya saukowa a sannan,saddi ne yana yima kansa komai don ba qaramin yaro bane bare tace zai nemi wani abu daga gareta,sai sultananta da tasan ita dinma indai ba wani abu ta buqata ba ba lallai ta nemi ganinta. Waya ta dauka ta kirayi bilki me aiki tace ta duba mata sultana ta dawo?. Ba jimawa ta sake kiranta
“Ta dawo hajiya”
“Yauwa to,ki bincika ko akwai wani abu da take buqata,idan babu shikenan,sai la’asar ni zan sauko”
“To hajiya” ta amsa mata a ladabce tana aje wayar. Mintuna biyu rak bilkin ta sake kiranta
“Hajiya qofarta rufe take” dan shuru ama tayi
“Lafiya?”
“Eh kaman lafiya gaskiya don na danji motsinta”
“To yayi,ki rabu da ita wala’alla hutawa takeyi,sai na sauko din”
“To a sauko lafiya” bilki ta amsa mata.
Wayar ta aje tana dan nazari kadan tare daci gaba da aikinta da take gab da kammalawa. Lissafin shekara shekara ne,wanda bayan ta kammala din take fidda zakka haqqin Allah.
Tana gamawa din yadda taso ta zauna ta huta sai tayi sallar la'asar kuma amma sai taji hankalinta yayi kan sultana. Kashe mini laptop din tayi,ta zura tausasan slippers dinta ta miqe tana nufo stairs din.
A nutse ta sauka ta kuma nufi sashen dakunan dake qasa. Tana ratsa falon suna gaisawa da masu aikinta da yau duka basu samu ganinta ba,tana amsa musu tana dosar dakin,har ta isa qofa.
Murdata tayi har yanzu tana kulle,ta kira sunan sultana din sau biyu bata amsa ba,sai ta juya yana yiwa fainusa magana kan ta duba store ta ciro mata spare key.
Cikin qasa da minti daya fainusa me aiki ta dawo da key din ta miqa mata,ta karba ta soma gwadawa har ta samu na dakin.
Dundum yake kamar ba rana ba,cikin mamaki ta kunna fitilar dakin haske ya gauraye,idonta ya sauka kanta sanda take nade tsakiyar gado lullube da qaton duvet. Mamaki ya kama ama ta kira sunanta tana takawa ciki hadi da cewa
“Bakijin zafi zaki rufa haka?,wanne irin bacci ne wannan sai an rufe kai?” Ta furta tana janye duvet din.
Razana tayi ganin yadda sultana din ke qudundune guri guda tana rawar sanyi sosai. Farar fuskarta ta sauya launi zuwa pink color kaman yadda tasan tanayi a duk sanda take zazzabi irin wannan ko wani ciwo. Tun bata kai hannunta ba take iya jin hucin dake fita daga jikinta gaba daya,duk da hakan sai ta miqa hannunta da sauri tana taba sassan wuyanta. Saukar hannun ama a jikinta sai taji kaman an qara mata ciwon,ta maqale wuyan wasu siraran hawayen suna fita daga idanunta
“Ya salam ya Allah” ama ta furta,zafin dake jikinta yayi yawa qwarai,sai ta dauki remote na ac din dake gefan gadon ta soma da kasheta,sannan ta juyo ga sultana din tana zama sosai a gabanta
“Dama dashi kika dawo daga makaranta?,tun yaushe ne?” Ta tambayeta cikin tsananin damuwa
“Tunda na shiga classe(class)” kai amma ta girgiza tana jin hankalinta yana daguwa
“Bari na kira Dr chafa’atou,zafin zazzabin yayi yawa” ta fadi tana sauka daga saman gadon sannan ta koma zuwa sassanta da gagggawa.
Qasa tayi da kanta tana lumshe idanuwanta bayan fitar ama. Wasu hawayen masu zafi kwatankwacin zafin zazzabin jikinta suka biyo kuncinta. Ita daya tasan me takeji cikin jikinta,tanajin kamar ana kama qasusuwanta ana ballasu daya bayan daya,kowacce gaba ta jikinta ciwo take mata sosai. Wasu sabbin hawayen suka kuma biyo idanunta,tun daga wancan ranar...... tun daga randa yayi mata fyade......tun ranar da ya zalunceta ya cuceta bata sake samun lafiya ba......bata sake jin qarfi cikin jikinta ba,ya tafi da dukka kuzarinta,ya tafi da walwalarta da kuma farincikinta,tana jinta a cikin jikinta ita karan kanta kamar ba sultanan bibi ba,kamar ba itace ke rayuwa a wannan gangar jikin ba.
Dukka wayoyinta ta debo ta dawo dakin tana gwada layukan wayar Dr chafa'atou. Bude qofar dakin ya sanya sultana bude fararen idanunta da suka sauya kala saboda tsabar zafin zazzafin dake fita a jikinta
“Sannu sultana…..sannu” ama ta fadi cikin kulawa ainun tana zama saman bedside drawer tana kuma sauraren wayar Dr chafa’atou dake ringing.
Dab da zata katse ta daga,cikin girmama juna suka gaisa
“Jikin patient dinki ne ba lafiya médecin(Dr)”
“Tofa,me ya sameta kuma?” Dr chafa’atou dake shirin zama saman kujerarta daga can cikin office dinta ta tambaya
“fièvre ne me zafi,dashi ta dawo daga école(school)”
“Subhanallahi,idan yayi zafi da yawa ki samu mouchoir(handkerchief) me kyau da ruwa a goge mata jikinta,gani nan na tashi gida zan wuce dama,zan qaraso na dubata”
“d’accord(okay),amma ina neman alfarma,zan saka motocin mayak’i yanzu suzo su taho dake,je ne veux pas de retard(banason jinkiri)”
“Hakan yayi ba damuwa” wayar dukka suka ajjiye.
Idanunta a lumshe,yadda jikinta ke zafi da quna haka zuciyarta,tana jin sanda ama ta iso da ruwan da qaramin towel ba tare data nema kowa ba
“Tashi a goge miki jikin sultana la fièvre est si élevée(zazzabin yayi yawa)” kai ta girgiza a hankali sannan tace
“A kiramin bibi,bibi nakeson gani”
“Za’a kirata,amma a ragewa jikin naki wannan zafin kada tazo ta gani hankalinta kuma ya tashi,ko kinaso hankalinta ya tashi kuma?” Kai ta girgiza a sanyaye,sannan ta yunqura ama na riqe da ita ta zaunar da ita sosai ta rage mata uniform din,ya zamana daga half vest din da ta soma kare martabar qirjinta da su,sai gajeran wando mahadin vest din. Sam ba wani kunya tsakaninta da ama,don ta zama tamkar uwar da babu shamaki a tsakaninsu. Tana goge mata din ta kirayi layin tanja donta kira bibi din bata sameta ba,tace ta shaida mata sultana ke rigimar son ganinta yau kuma,ta tashi da wani dan zazzabi. Tanja din ta amsa mata sannan ta kashe wayar ta maida saman drawer.
Tana gama goge matan akayi knocking qofar sannan aka turo. Bibi ce sanye da lallausan abaya cotton 'yar marocco ta mata me hade da mayafi.
Ama ce ta amsa mata tana miqewa hadi da tattare towel da roban ruwan,ta kuma jawa bibi kujera zuwa gaban gadon da sultana ke zaune.
Idanun bibi qur cikin na sultana bayan ta daidaita zamanta saman kujerar,sannan a hankali ta maida dubanta ga qirjin sultanan wanda ba baqonta bane.
Wata mummunar faduwar gaba ta samu kanta da ita
“La haula wala quwwata illa billa” ta fadi qasan zuciyarta,sannan ta janye idanunta ta juya zuwa ga ama dake qoqarin saqale towel din jikin qofar toilet
“Me ya sameta?”
“Zazzabi ama,daga tafiya makaranta”
“Zazzabi kawai?,kuma iya yau?” Ta tambayi ama cikin mamaki a sautin muryarta
“Wallahi bibi,kuma koda safen lafiya lau ta shiga ta miki sallama nima tayimin sallama,sun dawo nasa azo dubata su bilki suka samu qofanta a rufe,sai da na sauko dubata na sameta kwance” aman ta yiwa bibi bayani dalla dalla. Kai kawai bibi ta jinjina jikinta yana wani irin sanyi,dukka gwiwoyinta kamar an bubbugesu,wani irin fargaba ya cika mata zuciya,ta samu kanta tana furta addu’a can qasan zuciyarta……dai dai lokacin aka shaidawa ama isowar Dr chafa’atou wadda drivern mayak’i mansion ya daukota.
“Kiyi mata iso ta shigo” tace dame aikin nata tana komawa opposite bibi tana zama itama,jikinta yana sanyi da ganin sauyawar reaction na bibi cikin tambayoyin da tayi mata.
Har qasa Dr chafa'atou ta tsugunna ta gaida bibi. Sannan ta qarasa gaban sultana tana kallonta.
Kallo na kusan minti guda,kallon da ya sanya sultana janye nata idanun daga kan Dr chafa'atou,haushi yana cikata duk da ciwon da takeji a dukka gabobinta,don meye zata sakata gaba da kallo kaman taga wata dodo?.
“Bayan zazzabin kinajin wani abu dabanne?” Dr chafa’atou dake qoqarin bude dan akwatin aikinta ta fada. Da qyar ta motsa lallabanta ta bata amsa a gajarce
“Babu”
“Okay…..yaushe rabon da kiga period dinki na qarshe?” Tambayar da ta sake sanya razani me yawa a zuciyar bibi,ta kuma saka ama barin abinda takeyi tana duban Dr chafa’atou da batasan ma duka suna kallonta ba,don ita nata zargin yayi wani waje daban,don haka ta yankewa kanta yin abu guda daya da take da babban zato a kansa ba tare data batawa kanta lokaci ba.
“Bana tunanin zata iya riqewa,don kwata kwata al’adarta ma ina jin batayi yakai sau shida ba,niketa qoqarin tsara mata calendar dinta da sanar da ita lokaci donta dinga kiyayewa” bibi ta yiwa Dr chafa’atou bayani tana dubanta
“Okay ba matsala” ta amsawa bibi bayan ta gama fidda container dinta
“Kina Jin fitsari?” Ta tambayi sultana tana kallonta
“Kadanne”
“Yimin shi a nan koda dan kadan dinne” sai ta miqawa sultana container din.
Daga bibi har ama bin container din sukayi da.kallo,dukkansu sunsan gwaji akeyi da ita,kuma batun gwajin fitsari wani al'amari ne me zaman kanshi
“Amma ba fièvre du paludisme(zazzabin malaria) bane Médecin?(Dr)”
“Yanzun zamu gani in sha Allah hajiya” ba wanda ya iya sake cewa komai. Dr chafa’atou dince ta riqe hannun sultana har qofar toilet sannan ta dawo tana fidda kayan gwajinta. Duka duka bata wuce minti daya ba ta miqawa Dr din kwalbar ta koma saman gadon ta lafe tana rufe idanunta,don a yanzun babu abinda takeso da qauna irin ta ganta a kwance,cikin daki me qarancin hayaniya irin haka.
Duk motsin Dr chafa'atou suna biye da ita,har zuwa sanda ta kammala tsatsube tsatsubensu na likitoci,ta daga pt strip din da ya bayyana komai dara dara yana sake bata haske.
Saukeshi tayi tadan saci kallon ama da bibi,akaci sa'a dukkansu idanunsu yana kanta. Ajiyar zuciya ta sauke ta koma ta zauna,ita kanta tana jin fargabar bayyana sakamakon gwajin,amma kuma har kusan hada baki ama da bibi sukayi wajen tambayarta
“Ya dai?,an kammala?” Kai ta gyada musu,ta aro dukka jarumta da dauriya irin ta likitoci sannan tace
“JUNA BIYU GARETA!” Dif wutarsu ta dauke na dan wani wucin gadi,haka kunnuwansu suka tsaya da aiki na wucin gadin,kamar yadda kwanyarsu ta daina banbance saqon da aka aika mata dashi na wasu daqiqu. SULTANA dake a kwance kuwa taji dukka kalmomin Dr chafa’atou,amma abu daya zuciyarta da kwanyarta ta gaya mata
“Bafa dake take ba,magana take akan wata” wani sashe na zuciyarta ya gaya mata zuciyar na wani irin mugun bugu kamar ta balle daga qirjinta
“Kin duba da kyau kuwa Dr?” Ama data tattaro dukka sauran maqalallen busashen yawun dake saman halshenta ta fadi
“Na tabbata,a yadda kuma ya nuna shi sosai bana tunanin ma yana qasa da wata daya ne”
“Mun gode kawai Dr,tattara kayanki kije,banda rainin wayo ta yaya zaki kalli kaman sultana kice tana da ciki?, shekara sha ukun?,lallai na yarda da akace wani lokaci qwqwalwarku tana tabuwa” bibi ta fada da wani irin yanayi da zai gaya maka lallai ba cikin hayyacinta sosai take magana ba.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 page 16
"iya abinda na gaya muku hajiya bana tunanin akwai son rai a ciki ko kuma ba dai dai ba.....dukkanmu munsan me ya faru,ina ganin ba abu bane na mamaki don ance ciki ne da sultana ba......" Ta qarashe fadi cikin tausasa harshe da kuma dukka yunqurinta nason ganar da bibi abinda ke wakana.
Wani irin gumi ne yake yanko musu su dukka. Yayin da sultana dake kwance taketa qoqarin fasa maganar Dr chafa'atou cikin kanta. Wanne irin ciki take nufi tana dashi?,shin mene ne ma cikin wai?. Wani muguwar razana tayi sanda tunaninta yakai inda ya kamata yakai din,ita kanta batasan yadda akayi ta isa gaban Dr chafa'atou ba bare bibi da ama dake zaune kowanne jinin dake jikinsa nason daskarewa.
Kyakkyawan riqo ta yiwa Dr chafa'atou, muryarta da wani irin galabaitaccen amo......fararen idanunta da suka sauya launi dukka sun fito waje tana duban Dr chafa'atou,hucin da jikinta ke fitarwa bai damunta ko kadan
“Ba Bibi tace ki tafi ba?,me yasa kikeson sake jefani cikin halaka?” Ta jefawa Dr chafa’atou tambayar
“Don Allah medicin kice ba haka bane…..kice kuskure kikayi……me nayi miki zaki jawomin wannan abun?,ta yaya zan iya haihuwa?,kinga cikina fa dan qarami ne amma kike cewa wai ciki ne dani?” Ta sake fada tana sakin Dr chafa’atou,sannan taja da baya da wani irin hanzari tana tattare rigar jikinta har saman qirjinta,plate tummy dinta wanda ke shafe hade da bayanta ya bayyana. Daga jajayen idanunta tayi tana maida dubanta ga Dr chafa’atou dake tsaye tana karantar yadda kwanyar sultana din ke shirim birkicewa
“Kinga cikina?,ko plate din abinci daya bazan iya cinyewa…..amma kikayi qarya kikace ciki…….” Bata barta ta qarasa ba ta sanya dukka hannunta a tausashe ta jawo sultana cikin jikinta ta rungumeta tsam
“Kiyi haquri……wasa nake miki,kinyi qanqanta sultana,har yanzun ke yarinya ce” ta fada muryarta na rawa,tsananin tausayin sultana yana taba zuciyarta yana ratsa jikinta.
Daga bibi har ama gaza riqe hawayensu sukayi. Hawayen tausayin sultana,ta yaya zata iya karbar wannan qaddarar da qananun shekaru irin haka?,ta yaya zata iya fuskantar wannan qaddarar cikin rayuwarta?,ya rayuwarta zata zama?,ciki a shekarun da duka duka basufi sha uku zuwa sha hudu ba.
Sun jima a haka dakin tsit,bakajin komai sai sheshsheqar kukan sultana,wanda tun tanayi da ragowar qarfin da ya ragewa jikinta har ya zama bata iya koda motsi saboda wani mahaukacin zazzabi da yafi na baya daya sauko ya rafketa.
Cikin hanzari Dr chafa'atou ta fara bata taimakon gaggawa don kada zafin zazzabin ya kaita ga convulsion musamman da yake ba ita kadai bace,zazzabin zai iya zama illa ga abinda ke mahaifarta,duk da cewa ta lura har yanzu bibi ko kadan bata yarda da abinda ta gaya musu ba.
Kimanin awa daya kafin bacci ya dauketa,don Dr chafa'atou ta sanya ruwan allurar bacci cikin ruwan,saboda a yanayin da take ciki yanzu bacci ne kawai maslaha.
“Zan wuce,Allah ya bata lafiya,saidai koda baki yarda da abinda na fada ba yana da kyau a kula da lafiyarta,a sake gujewa sanyata damuwa” tayi musu taqaitaccen bayani dukansu da ama da bibi din.
Qwaqwwaran motsi aka rasa wanda zaiyi a cikinsu,ta tafi ta barsu da tarin tunane tunane qulle qulle da kuma kwancewa. Ita dai ama bata da abinda zata iya cewa bibi,maina ya tafi ya barta da dukkan wani nauyi da kuma kunya. Yayin da Bibi take juya maganar Dr chafa'atou wadda take jinta kamar a duniyar mafarki.
Shigowar aba dakin shi da goumar shi ya katse shurun da yake wanzuwa a dakin tsahon wani lokaci. Dukka suka daga kai suna amsa sallamar tasa yayin da nashi idanun suke kan ledar ruwan dake shiga jikin sultana.
“Dama bata da lafiya?” Yayi tambayar wa bibi. Da qyar ta iya buda fatar bakinta guda biyu tana gyara qafafunta da sukayi tsami
“Dazune kawai bayan fitarta makaranta”
“Subhanallah” aba ya furta bayan ya isa gaban gadon yana taba temperature na jikinta wadda ta fara sauka
“Allah ya sawwaqe ya taqaita gaba……amma ba damuwa bace har yanzu a ranta bibi?” Ya sake yin tambayar yana waiwayowa hadi da duban bibi.
Kai ta girgiza da qyar kamar me ciwon wuya alamun a'ah
“Wannan abinda ke damun nata a yanzun yafi qarfin damuwa muddin abinda Dr chafa’atou ta fadi gaskiya ne……muddin abinda tace yana damun nata da gaske ne dukkanmu muna cikin tashin hankalin da bamusan inda zamu ajeshi ba,bakuma musan da wanne ido mutane wadanda basusan sultana matar maina bane zasu kallemu” tamkar an doke masa gwiwa haka yaji,sai ya qaraso gaban bibi din ya zauna sosai saman qafarsa yana kallonta. Tun daga zuciya zuwa ruhinsa addu’a yakeyi, ubangiji yasa ko meye kunnuwansa zasu jiye masa yanzu su jiye masa sassauqar qaddara
“Ya salam…….wani mummunan ciwo ya shafa mata?” Tambayar da yayin sai data motsa ran ama. Tayi qasa da kanta tana jin babu dadi,yaronta kamammen mutum ne wanda tsahon zamanshi dasu ko sau daya basu taba gani ko jin labarin ya tsaida yarinyar kowa bama,amma me yasa tunanin aba koda yaushe ke zarga masa mummunan zato game da maina din?,dan cikinsa?,me matuqar masa biyayya?,don kawai Allah ya kawo tsausayin faruwar wannan abun?.
“Ba ciwo bane,juna biyu gareta wai” qas aba yayi da kansa zuciyarsa na cika da wasi wasi. Ko kusa ko alama baiyi tunani ko tsammanin jin haka ba. Maganar shima sai tayi masa nauyi,bakinsa kuma ya sarqafe ya kasa furta komai.
“Inaso gobe ni dakai da ita muje wani asibitin a sake gwadata,don inason sanin gaskiyar batun” ta fadi da alamun da gaske take maganar tun daga zuciyarta har harshenta
“In sha Allah”.
Dukka sauran maganganun ama tana ji batace komai ba,nata tunanin yayi nisa ne kan yadda rayuwa zata kasance a garesu gaba daya. Batasan ME GOBE TA TANADAR MUSU BA.... BATASAN ME K'ADDARA TA AJIYE MA GOBENSU BA......yadai tabbata GUDUN K'ADDARA GUZURIN TADDATA CE.......
****Dogon lallashi wayo da dabaru tayi kafin ta samu nasarar da sultana tayi wanka. Ta tabbatar a yadda jiya aba ya kwana da zancan cikin ranshi zaiyi wuya basuyi fitar safiya da ita yawon gwadata ba.
Breakfast me kyau kamar kullum ta shirya mata da kanta. Ta sameta zaune tsakiyar gadon. Gaba daya ta jeme ta lalace,tun daga wancan lokacin sultana bata sake kyawun gani ba,ta firje ta firgice,tsakanin jiya zuwa yau kuma gaba daya ta sake zama kamar wata susutacciya.
Da kanta ta zauna ta fara bata breakfast din bayan ta sha kanta. Saidai loma daya kacal ta fara kelayowa ama amai kamar me shirin amayar da dukka kayan cikinta. Hankalin ama din ya tashi qwarai ganin yadda take maida numfashi kamar wanda ke shirin qwace mata. Ita ta gyara wajen tas ta kuma gyara mata jikinta,sannan ta sauya mata wasu kayan.
Zaune tayi kawai gaban sultanar wadda keta rera kuka da galabaitacciyar muryarta. Abinda takeji din tunda aka haifeta bata taba jin makamancinsa ba,wani irin ciwo takeji da rashin dadi da sukuni,dukka duniyar takejin ta mata wani irin zafi kamar ma ta mutu ta huta,ba abinda takeso,babu kuma abinda yake burgeta.
Sau uku tana bude bakinta da zummar baiwa sultana haquri sai kuma taga na meye?,me zata cema sultana din?,babu wata kalma a yanzu da zata gayawa sultana da zata cire mata radadin da takeji yanzu a qirjinta. Laulayin cikin ba qaramar masifa bace ga duk macen da Allah ya jarabceta dashi. Inda idanun bibi a bude suke bata makance da son jin akasin gaskiya ba tana tunanin yaci ace ta fahimci da gaske ciki ne da sultana. Jiya bayan duk sun fice sun barta daga ita sai ita ta qarewa sultanar kallo. Komai nata ya canza,hatta qirjinta da suke matasa zuwa yanzu sun fara cikowa,abinda dukkansu suka makance idanuwansu basukai ga ganinsu ba. Dukkansu ubangiji ya kauda hankalinsu daga ganin wannan,sai a yanzu da yaga dama ya bayyana abinsa.
Saddi ne ya shigo a hankali idanunsa akan fuskar sultanan. Shi kansa mugun tausayinta yakeji,yakan kuma tambayi kansa kuma ME YA MAINA YAYI MATA NE WAI?,ME YASA YAYI MATA ABINDA YASAN BATASO?.
“Aba yace sultana ta fito” kai ta daga ta kalleshi
“Kace masa gata nan zuwa,zataci abinci ne” amsawa yayi ya juya ya fita. Shuru tayi tana tunanin me zata bata?,kaf tunaninta a yanzun bawai gudu yakeyi ba,batasan me zata bawa ‘yar marainiyar Allahn da zai riqeta ba. Wani tunani ne ya fado mata,ta tuna abinda nafessa tafi yawanci sanda tana da cikinta,may be idan tayi gado itama ta iya ci din.
Cikin mintuna ta kammala ta dawo ta sameta,har yanxu kukan takeyi da wani irin rashin kuzari.
“Taso kiji sultana” ama ta fadi tana zama kusa da ita tare da dagota. Sanda takai spoon din kusa da bakinta kai ta girgiza tana kauda kai
“Don Allah ba don ni ba ki karba” karon farko da ama tayi mata magiya tsahon tarayyarsu,sai taji nauyinta ya kamata. Hidima take mata tsahon dare da wuni,duk da tarin ‘yan aikin dake sassanta amma ta maida hidimarta saman wuyanta kamar yadda hidimar aba ta zame mata dole,batajin koda su saddi da suka fito daga tsatsonta sun samu nau’in kulawar da take samu cikin wata ukun daga wajen ama,wannan ya sanyata bude bakinta zuciyarta na mata nauyi.
Batayi tunanin ko Loma biyu zata karba ba,amma sai gashi har takai biyar,ata shida ta kauda kanta hawaye naci gaba da tsartuwa daga idanunta. Ko iya hakan da taci ya yiwa ama dadi,tasan dai aqalla dai ba za'a ce babu komai cikin cikinta ba.
Hijabi me kyau a tsaftace ta fiddawa sultana,ta sanya mata sannan ta bata takalmi ta saka ta sakata a gaba zuwa parking lot na gidan.
Acan ta samu oncle bashar oncle umar da matansu. Batace komai ba ta budawa sultana bayan motar inda bibi ke zaune ta sakata
“Duk inda kikaji kin gaji ki samu waje ki zauna har sai jikinki da yanayinki ya daidaita” abinda ta cewa sultana kenan kawai ta juya tana barin wajen ba tare da tace da kowa komai ba,ba kuma tare da tayi tayin binsu din ba,saboda tasan yawo ne kawai zasuyi tare da batawa kansu lokaci.
Abu daya data sani shine,ko kadan a zuciyarta bataji tana qyamatar cikin da sultana ta samu ba,bata kuma ji baqinciki ba,kawai dai ta razana da jin sakamakon……tana kuma tsananin tausayin sultana da ciki a qarancin shekarunta.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 17
Tunda ta koma ciki wayarta ke hannunta,sai tayi kaman zata kira bibi ko aba din sai ta fasa. Haka kawai takejin zafin yadda suka dauki abun da zafi suka girmameshi haka,a nata zaton yau ko fyaden da babu aure maina ya yiwa sultana,sannan har rabo ya shigo ciki,tayi zaton zasu karbi abun da sunan qaddara,su kuma rufa abun don yiwa juna halacci da kuma kyautata alaqar juna tare da girmama tsatso.
Daga qarshe data gaji da kai kawon da bashi da amfani sai kawai ta shiga kitchen da kanta. Dukka masu aikinta suna ciki,kowacce na hidimar da take alhakinta ce. Cikin girmama suka matsa suna bata hanya. Bilki ce ta fara tambayarta
“Ko akwai abinda kike buqata?” Kai ta girgiza
“Ba komai,zan dan gwada wasu qananun abinci ne ko za’a dace sultana ta samu wanda zata iya ci a ciki kafin su dawo” . Bata bawa kowa aiki ba,tace dai kowa yaci gaba da aikin dake gabansa.
Tana aikin amma sam ko qananun hirarrakin dasu bilki keyi a tsakaninsu bata iya tantancewa,saboda tsabar nisan da tunaninta yayi. INA MAINA YA TAFI?,wasa wasa kwanaki nisa suke suna kuma jirkicewa zuwa watanni,a ina yake?,ina yaje?. Ba qaramin damunta abun yakeyi ba cikin rai,a duk sanda ta sanya haqarqarinta a qasa zata kwanta maina dinne yake soma fado mata. Abinda ta lura ko sau daya aba bai taba tada maganarsa ba,sau biyu oncle umar da oncle bashar suna masa maganar sai yace dasu
“Ai ba yaro bane shi,ya fita sahun yara ko samari,magidanci ne yanzu,duk inda yaje ma zai dawo da qafafunsa,bani da lokacin bata lokaci wajen nemansa” itadinma ko sau dayan batayi gangancin masa maganar ba,tana iya nata qoqarinne kawai a bangarenta wajen samun koda labarin inda yake.
Shuru office din likita na uku da suka ziyarta a ranar yayi. Asibiti na qarshe da dukkansu sukayi yaqinin ba inda za'a gaya musu sama da abinda zasu gaya musun,saboda qwarewa da ingancin asibitin da har takai bayan ainihin asibitinsu Dr chafa'atou shine asibiti na biyu da ya samu lambar yabo daga qasar France,suke kuma da qwararrun likitoci da wasunsu 'yan asalin qasar France dinne.
Kanta na kwance saman kafadar bibi tana wani irin kuka kamar numfashinta zai dauke. Aba dake zaune ya gaza cewa komai,saidai dukka hankalinsa yana kan mahaifiyarsa saboda dimbin tashin hankalin da ya gani saman fuskarta. Shekarunta sun fara jaa,yana tsoron kada wani ciwon ya sarqafeta.
“Wannan kukan da takeyi yayi yawa,yanzu haka da na duba awon jininta,jininta ya hau daga qa’idar yadda ya kamata ya kasance,tana buqatar kulawa ta musamman,saboda shekarunta sunyi qanqanta qwarai da iya rainon juna biyu,muddin anason ta rayu lafiya ita da abinda yake cikinta dole a kula da damuwarta” kai bibi ta girgiza
“Ba zamu taba iya hanata wannan kukan ba…..mu dinma inda da hali barin namu idaniyar zamuyi ta zubda qwalla……. abu daya kawai na sani……bazan bari rayuwarta ta galabaita ba muddin ina numfashi” bibi ta fada da qwarin gwiwa.
“Yanzun zamu dan riqeta saboda tana da buqatar kulawar likita gaskiya qwarai da gaske,zamu sanya mata ruwa saboda jikinta babu isashen ruwa,sannan hawan da jininta yayi ma banajin yana da kyau a qyaleta ta tafi gida,akwai gwaje gwaje da dukka za’a yi mata a ajjiye koda buqatar gaggawa zata taso”. Yana kaiwa nan nurse din ta shigo cikin harshen faransanci take gaya masa sun gama shirya komai
“Ku rakata dakin” ya fadi yana hada tarkacensa dake saman table din.
Tashin hankalin da takeji ya zarta duk yadda zata misalta. Sanda ta miqe nurse din ta kama hannunta sai taji ba zata iya sakin hannun bibi ba,a hankali taji idanunta sun soma rage kaifin ganinsu,wanda guda dayan da aka yi mata glasses saboda shi zuwa sannan ya sake samun raunin gani sosai sakamakon hawayen da take wuni ta kwana tana zubdawa. Babu wata ranar banza a gareta da zata fito har ta fadi hawaye basu fita daga idanunta ba.
“Muje ko?” Nurse din ta fadi cikin kwantar da murya. Qoqari take taga ta taka amma sai taji qafafunta kamar an riqesu,qirjinta kamar an aza masa wasu kaya masu nauyi,kanta kamar an daketa da wani qaqqarfan abu,duhu kuma ya soma mamaye hasken tarwai da office din yake dashi,ba tare data shirya ba hannayenta suka zame daga cikin na bibi,babu abinda taji sai salatin bibi da wani irin qaqqarfan sauti.
****Tamkar wadda ake tasa daga bacci ta soma bude idanunta,wanda tun kafin takai ga gama bude idon gaba daya ta danji muryoyin qasa qasa. Sannu a hankali ta gama bude qwayoyin idanunta,fes suka sauka cikin dakin.
Mutum biyu ne zaune gaban kujeru ukun dake gaban gadon nata,sai kuma oncle umar da oncle bashar dake tsaye daga saman kanta. Saitin qafafunta kuma mamma kausara ce(qanwa ga mahaifinta hamani uwa daya uba daya).
Kusan kowa yunqurin mata sannu yakeyi,yayin da ama da mamma kausara suka matso suna qoqarin tadata zaune ganin tana mutsu mutsu
“Dole ki gaji,kwanciya ace tun jiya?” Ta danji mamaki cikin ranta,to amma kuma a yanzun ita duka ba wannan bane gabanta ba.
Duk sai da suka gama mata sannu da jiki sannan ama ta kawo ruwa ta bata. Tasha da yawa sosai,sannan ta kamata ta sauko da ita zuwa bandaki
“Kiyi wanka kizo ki rama sallolin da ake binki ko da a zaune ne” ama din ta fada.
Tayi wankan ta kuma rama kuma sallolin,saidai daga haka ba abinda ta iya qara yi,tana daga zaune saman abun sallar kawai. Ita ba tunani ba ita ba bacci ba, hakanan ita ba ido biyu ba,a haka 'yammatan gidan sa'anninta sukayi sallama suka shigo.
Aminata,yasmine,najma almu sai atta biye dasu. Sai da suka gama gaida iyayensun sannan suka qaraso inda take zaunen. Zagayeta sukayi kowa yana mata sannu cikin nuna kulawa da qauna ta 'yan uwantaka.
Banda kalmar DA SAUQI ba abinda ta iya sake furtawa. Da idanu kawai take binsu wani abu yana kai kawo cikin zuciyarta,sai kawai ta hade qaffaunta waje guda tana cusa kanta tsakanin cinyoyinta,don kuka take da buqatar ta sakeyi. Wannan kukan batasan yaushe zata daina yinsa ba tsayin rayuwarta,su aminata sha'awa suke bata,tana jin dama itace su,su dinma kamar haka rayuwarta take a baya ba?,tashi daya zallar zalunci irin na maina ya kutsa rayuwartata ya wargaza mata komai ds komai,ya rusa farincikinta da walwalarta,yayi rugu rugu da mafarkinta,a yanzun bata da wani sauran mafarki ko buri na rayuwa,tana jin rayuwarta dai dai take da fanko,tana kunyar kallon idanun su aminata su hanan da sauran qawayenta su ganta dauke da wani abu waishi CIKI!,cikin da suke gani jikin yayyensu?,cikin da suke ganin jikin iyayensu?. Batasan ya akayi sautin kukanta ya fita ba,saiji tayi su yasmine suna rungume da ita suna bata haquri,dukka muryoyinsu suma a karye,abinda ya sanya bibi miqewa kawai ta fice a dakin.
****Dukkan iya abinda likitoci zasu yi mata na taimakon da ya dace sun bata,saidai kuma jigon samun sauqinta yadda ake da buqata yana hannunta.
Nutsuwa kwanciyar hankali da taqaita damuwa,abubuwa ne kuma da zasuyi wuyar gaske ace an samesu daga wajenta a yadda take ciki a wannan lokacin.
Wani irin matsanancin laulayi mai matuqar azabtar da ruhi da gangar jiki. Ta fita hayyacinta ainun,tayi wata irin rama da bata taba kwatankwacinta ba,har takai jallin da dukka suturunta sunyi mata yawa basa sanyuwa a jikinta. Bata iya cin komai,hakanan bata iya shan komai,kusan qarin ruwa shine abinda akafi yi mata duk bayan kwana biyu saboda samarwa jikinta abinci.
Wannan yanayin ya daga hankalin bibi matuqa,ta dinga jin kamar lokacin da zata rasa sultana ne yayi,kaman yadda ta rasa MOHMOUD ta rasa BINTOU ta kuma rasa NAFESSA. Wannan tunanin yayi matuqar razanata,ya kuma sanyata tattara dukka 'ya'yanta harma da ama da kuma mamma kausara ta shaida musu hukuncin da ta yanke ba kuma tare da neman shawararsu ba. Shawarar da take ganin ita daya ce MAFITA,ita kadai ce kuma hanya ta yankewa wannan AZABA da sultana ke sha, sa'annan qilan ta zama silar warwarewar bakin zaren komai.
***A ranar data nemesun ta shaida zamanne bayan sallar isha’i. Cikin daya daga cikin falukanta masu kyau da tsari,wanda sam basu cika girma ba,sannan bata fiya wani zama cikinsu ba saboda ba falo bane dake a farko farkon sassanta ba.
Ama ce qarshen shigowa,sai data tsaya ta tabbatar abu me ruwa ruwa ya shiga cikin sultanan bayan wunin da tayi a wunin yau sur bata sanya komai a cikinta ba,sai uban amai da ya galabaitar da ita liqis. Duk sanda ta tashi da rikicewar yanayi irin hakan wuni ama din takeyi itama cikin tashin hankali. Tuntuni ta sauke dukka wasu harkokin business dinta ta damqawa wasu daga cikin mataimakanta,sai kuma saddi da yake yaayan atta da almu data dora masa wani nauyin shima,duk kuwa da cewa shekarunsa ba wasu masu yawa bane,duka duka sha bakwai yake amma lalura ta sanya dole ta fara dorashi bisa hanya.
Ta samu tasha oat da madara dan qaramin cup da baifi cup din yaro dan yaye ba,saidai duk da haka ama murna takeyi da ya zauna acikinta har ma bacci ya dauketa.
Tun jiya da bibi ta shigo wajen sultana,ta kuma buqaci ama ta basu waje zasuyi magana taji hankalinta bai kwanta ba. Duk wani kuka da damuwa da take ciki babu shi daga jiya zuwa yau din,sai laulayin kadai dake hanata sukuni. Maganar qarshe da taji bibi na fada bayan ta dawo canzawa sultana beadsheet ta tsaya mata a rai,ta kuma dinga juyata cikin ranta. Ta qure dukka maqurar tunaninta wajen son gano abinda maganar ke nufi,amma mahanga daya kwanyarta ke kaita,a ma'ana daya duk wani ma'aunin fassara yake zuwar mata,ma'anar da taqi gamsuwa da ita,zuciyarta taqi aminta da hakan.
“Karki damu,kwana uku kawai zakiji sauqi ki koma rayuwa kamar ‘yan uwanki,duk wani ciwo zai wuce” to meye qarshen maganin laulayi haka da gaggawa?,laulayin da ba abu bane me yankewa yau ko gobe ba?,har sai sanda rabbi ya dauke maka,ko kuma zuwa sanda ka haife abinda yake cikinka?.
Da sallama ta shiga falon,sai taga kamar dukka idanu sunyo kanta. Bata wani bada muhimmanci ba ta qarasa daya daga cikin kujerun dake daura da aba,ta dauke filon kai ta zauna,ta kuma gyara zamanta sosai tana fuskantarsu
Tofa!,taron na meye?,me karatu muje zuwa,akwai sauran tirka tirka
wai ina Aliyyu haidar ya shiga ne?,ko team SULTANA NE SUKAYI MASA KURCIYA?🫣🫣🫣
HUGUMA CE
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 18
“Tom,nasan dukkanku kuna mamakin abinda yasa na taraku a nan wajen?……a taqaice ba wani doguwar magana bace me tsaho,sannan kuma ba shawara na taraku nayi daku ba,na kiraku ne don na shaida muku,babu buqatar cikin dake jikin sultana a yanzu,saboda dukkaninmu munsan abinda likitoci suka fadi gami da hatsarurrukan dake tattare da lafiyarta,kuma ita din munfi buqatarta akan abinda take dauke dashi,saboda haka na yanke shawarar aje A CIRE CIKIN JIKINTA ma’ana A ZUBAR DASHI! don ta tsira da rayuwa da lafiyarta” Dif dakin ya sake yi,kowa ya zubawa bibi idanu sona son gano wasa takeyi musu?,ko tana fadin maganar ne da gaske.
Kaf dinsu babu wanda yaga digo ko alamun wasa tattare da bibi din, fuskarta ta sauya zuwa wani yanayi da yake sanya musu shakka a duk sanda wani ya yunqura zaiyi jayayya da umarninta. Ba wanda baiji saukar maganar har tsakiyar zuciyarsa ba. Kusan daqiqa uku kowa ya gaza tofa komai kafin daga bisani oncle oumar ya motsa yana matsowa gaba kadan daga kan kujerar da yake zaune
“Amma bibi……” Hannu ta daga masa tana cewa
“Dakata oumar,ya isa,bana buqatar qarin bayanin kowa,inajin dukkaninku ba wanda yasan ciwon sultana sama dani…….”
“Sai kuma maina…..wanda shine yaci kashinta yaci fitsarinta,shine wankanta shine wankinta,tare suke jinya kukanta nashi ne damuwarta tashi ce……. shine cikinsa yake a jikinta a yanzu…..cikinsa na halak ba shege ba…..cikin da baya biya sadaki da albashinsa na dan makaranta…..shine cikin da ake cewa yanzu a cireshi?” Ta qarashe maganar tana jefawa bibi tambaya
“Hamdiyya…… meye haka?,kinsan a gaban wa kike a tsaye?,kisan me zaki fadi……”
“Me zan fada?,me zan fada ma?,to ban qarasa ba…….indai nice mahaifiyar Aliyyu,kuma akwai haqqinsa a wuyana,akwai kuma nawa haqqin a wuyansa…..ina fada da harshensa da nawa……ban yarda a fidda abinda yake tare da sultana ba,ban yarda ba har abada……..!” Saita qarashe da wani kukan da bata shiryawa ba ya kufce mata,sai ta juya da gudu gudu sauri sauri tana fita daga falon,tana jin qirjinta yana mata nauyi,wani abu ya tokare mata qirjinta.
A gurguje a gurguje ta dinga ratsa farfajiyar gidan har ta isa sassanta. Can cikin dakinta ta yiwa kanta masauki,ta zube daga bakin gado a qasa kuka yana qwace mata.
Shin ta yaya?,ta yaya ma zata bari a zubda cikin aliyyu?,da wanne dalili zata bari hakan ta faru?,koda cikin shege bare na halak?,idan su dukka tunaninsu ya toshe hankalinsu ya gushe da soyayyar sultana don kawai su sama mata mafita to ita din tana a dai dai cikin hayyacinta.
Tayi kukan data jima batayi irinsa ba,ta kuma jima a nan zaune tana tunanin hanyar ra zata hana faruwar abinda bibi ta qudurta. Ta sani ta kuma yankewa ranta ko a mutu ko ayi rai,koda igiyar aurenta zata girgiza ba zata taba bari wannan abun ya faru ba.
Sanda ta kalli agogo sai ya nuna mata qarfe biyu da rabi na dare. Ta share sauran qwallar da suka rage mata cikin idanunta tana miqewa. Mafita guda daya ce yanzu tak ta rage mata ta amintar da sultana takuma sauketa daga doron amincewar da bibi ta sanyata tayi kan a zubda cikin.
Bandaki ta nufa ta daura alwala saboda ta samu sassaucin abinda takeji tsakiyar qirjinta,sannan ta fito ta dauki medium veil me santsi mahadin rigar jikinta ta yane kanta,ta jawo wayarta ta kunna data sannan ta nufi qofa ta buda a nutse ta fice a dakin.
Sau daya tak ta murda qofar dakin ta bude,saita tura a hankali tana shigewa. Fitilar gefan gado ne kawai a kunne,saman gadon kuma babu kowa alamun sultana din ta tashi,sai ta zauna saman sofa bed din dake daura da ita tana jiyo motsin ruwa a bandaki,sai ta tattara hankalinta akan wayar tana ci gaba da research kan abinda take da buqatar
A nutse ta kammala fitsarin tayi tsarki,saita matsa gaban wall mirror dake jikin bandakin,ta murda famfo ta wanke fuskarta da kyau,bayan ta gama taja qaramin towel ta soma goge fuskarta,a sannan ne idanunta suka fada kan fuskarta data fito tarwai ta cikin madubin kamar rana saboda wadatar haske da bandakin yake dashi.
A hankali take qarewa fuskartata kallo,fuskar da aqalla ta dauki watanni sama da uku rabon data kalleta. Lumshe idanunta tayi tana jin ciwon yadda dukka kamanninta suka canza,ta sanya hannu a hankali ta shafa gefan idonta da har yanzu akwai sauran tabo na bahagon marin da ya kaiwa fuskarta har ya zame ma idanunta illa. Janye hannun tayi tana jin wata irin mahaukaciyar tsanarsa tana ambaliya cikin zuciyarta,nau'in tsanar da tunda tazo duniya bata taba jin digo ko kwatankwacinta cikin ranta game da wata halitta ba.
A hankali sai kuma takai hannunta saman shafaffen cikinta. Itakam har yanzu bata yarda da zancan wai ciki gareta ba,bataji cikinta ya dago ba,bataga ya qara girman komai ba,hakanan batajin komai banda qinson cin abinci da dan banzan fitsari da take yawaita tashi cikin dare,sai kuma rashin lafiyar da ai ita dai tasan normal ne kowa yana iya cuta.
Kamar kuwa jira akeyi takai qarshen tunanin nata taji wani abu ya harba sau biyu a marartata kwatankwacin bugun zuciya. Ta miqa hannu da sauri dai dai gurin ta danne tana zare ido tare da saka ran sake jin wani abu. Saidai kuma tsayin sakanni shuru bataji komai ba,wannan ya sanya ta saki hannun nata hawaye na cika mata idanuwa.
Indai da gaske ne cikinne ita wallahi babu abinda zatayi dashi,d'an maina ne fa kenan ko?,ita zata haifawa baqin mugu azzalumi yaro?,sun hada jini kenan kamar yadda taji ana fada?,Allah ya kiyaye ya kuma sawwaqe ta hada jini da maina,la shakka shawarar bibi itace dai dai,bibi din masoyiya ce ta gaske,wadd bata qaunar kukanta ko damuwarta,batason dukkan wani abu da zai zamewa rayuwarta barazana,tsahon shekaru tana akan haka. Towel din ta maida cikin zafi tana jin cewa gari yana wayewa zata buqaci bibi ta kaita a cire d'an aliyyu daga jikinta,ta tako da kuzarinta daga bandakin tana fitowa.
Tsaiwa tayi daga bakin qofar cikin mamaki tana kallon ama wadda ke zaune sosai cikin dakin,ta kuma qarawa dakin haske da qwayaye biyu dake manne a bango gudun kada sultana din ta tsorata. Idanu ta daga daga inda take zaunen tana duban sultanar,sai ta gyara zamanta tana cewa
“Qaraso ciki,nazo dubaki ne na tarar bakya ciki” sakin qofar tayi tana takowa cikin dakin,har cikin ranta tana jinjina tsantsar kulawar da ama ke bata,ta yadda da wannan dari bisa dari, kowanne motsinta ama na dame dashi,ko yaya kuma ta sauya tana riga kowa fahimta ta kuma bi ba’asin matsalar ta maganta mata.
Wayar hannun nata ta ajjiye bayan sultana din ta zauna tana dubanta
“Sultana,magana nazo muyi dake,ki nutsu sosai ki fahimceni kinji?” Kai ta gyada a hankali tana kallon qwayoyin idanun ama
“Me yasa kikeso ki MUTU?” Ama ta jefa mata tambayar kai tsaye,tambayar data saka sultana zaro fararen idanunta tana duban ama a rude
“Ni kuma ama?,ni nakeso na mutu?,banaso na mutu ama……”
“A’ah,qarya kikeyi,keda bibi duka so kukeyi ki mutu” sake rudewa tayi ainun,saboda kalmar mutuwar girma take mata
“Allah a’ah ama,banaso”
“Amma kikeso a zubda miki ciki?,bakisan duk wadda aka zubarwa da ciki mutuwa takeyi ba?” Tsam tayi tana duban ama hawayen nan nata da basu da wuyar fita tana zartowa daga idanunta. Tsaf ama ta karanceta,da alama abu ya fara tabata,saita dora da cewa
“Ungo wannan ki gani,ki kuma karanta,adadin mata nawa ne suka mutu duk akan silar zubda ciki” hannu tasa ta karba din,ta shiga folder din da ama ta shirya komai ta soma kalla wani kuma ta karanta bayanan da suke da harshen France.
Bata iya qarasawa ba cikin matuqar tsoro da razani ta miqawa ama wayar hannunta yana rawa,ama tasa hannu ta karba tana dorawa da cewa
“Dukansu KARUWAI ne sultana, ba’a daura musu aure da ubannin masu cikin ba,me zai kaiki layin karuwai?,don kawai kin tsani MAINA……”
“…….ama don Allah,daina kiran sunansa” ta fadi da sautin kuka sosai,tana jin mafitar da take hango qofarta a bude qofar ta ida rufewa ruf,gaba kura baya sayaki,ashe sauqin da take hasashen samu babu shi,ta tsorata da irin bayanan data gani,itakam ya za’a yi taso ta mutu haka?,da irin wadannan shekarun qanana?.
“Na daina kiran sunansa sultana,kiyi haquri……amma…….ki share hawayenki,ki kuma bani aron hankalinki nan” shuru ya ratsa dakin na wasu mintuna sultana na qoqarin saisaita kanta sannan tadan samu ‘yar qaramar nutsuwa
“Kin yarda bakison ki mutu?” Ama ta tambayi sultana. Da sauri ta daga mata kai
“Amma tunda bibi tayi zancan bansan ta yadda zance mata kada a zubar ba”
“Ni nasan yadda zan hana haka faruwa don banason ki mutu,abinda nakeso kawai shine,kibar cikin ki haihu,zan karbi ko meye kika haifa ke kuma kiyi tafiyarki kiyi rayuwarki babu me takuraki,kinga shikenan babu ke ba mutuwa”
“Amma wajen haihuwar ai ake mutuwa ama” ta fada da sautin quruciya fal muryarta
“Inji wa?,inda haka ne suk da bamu haifeku ba ai ko?,waye a cikin gidannan kika taba gani ya mutu don zai haihu?” Shuru tayi tana son tunawa. Babu,babu wadda ta gani ko ta sani iya wayonta da akace ta mutu wajen haihuwa,amma wajen zubda ciki kuwa gasunan yanzun ta gansu da idonta bila adadin.
“Kin yarda zakibi dukka tsarina ni kuma na tsallakar dake daga fadawa mutuwa?” Duk wanda zai kauda maka mutuwa aiba abun gudu bane,bare ama din da zuwa yanzu take jinta kamar mahaifiyar data haifeta,don haka ta gyada mata kai
“Da kyau,amma abinda nakeso fa dake shine,kada ki gayawa kowa wannan maganar da mukayi dake kinji ko?,idan ba haka ba zasu daukeki sukaiki gun cirewa da wurwuri kafin na gama nawa tsarin”
“To ama”
“Yayi kyau,maza kwanta sai da safe,kada kuma kiqiyin bacci kinji ko?komai zai wuce in sha Allah” Kai ta jinjina mata. Ama bata bar dakin ba sai data tabbatar ta kwanta,ta kuma lullubeta ruf sannan ta kunna mata karatun qur’ani da madaidaiciyar qira’a ta kashe hasken dakin sannan ta fice.
A daren bata kwanta ba sai data ci rabin plan dinta,don tana ganin tana kwanciya kamar lokaci zai qure mata,don bata da isashen lokacin gama komai da komai da takeso.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 19
A daya daren kuma ta kammala shirinta gaba daya,cikin daren da kowanne ya kwanta a cikin gidan,daren da suke sanya ran washegarin safiyar ranar za'a fita da sultana a zare tayin cikin......a daren ta shammaci kowa a cikinsu,harda 'ya'yan cikinta saddi da almu,a daren dai ta fice daga gidan,ITA TANJA DA SULTANA ba tare da sani ko ankarewar kowa ba.
K'arfe sha biyu na daren ranar amma tamkar rana ce cikin zuciyar ama. Mace mai kamar maza wanda ko sau daya tun daga quruciya zuwa girma zuciyarta batasan karaya ko tsoro ba. Ita ke tuqa motar da hannuwanta ba tare data dorawa kowa nauyin tuqata ba bare a buqaci sanin ina ya kaisu?.
Gudu kawai take shimfidawa cikin lafiyayyar motar tata,sultana na bacci abinta lakadan a baya,tanja na zaune daga gefan ama din tana rarraba idanu. Har yanzu cikin fargaba ita take,ga tsoron daren da suke ketawa saman shimfidaddiyar kwaltar da zata sadaka har cikin qasar nigeria.
“Ki saki jikinki tanja,ba abinda zai biyo baya sai alkhairi,ba kuma abinda zaya faru” ama ta fadi idanunta nakan kwalta data cika da full light na fitilun motar masu tsananin haske. Ajiyar zuciya ta saki tana gyara zamanta
“Amma hajiya,bakya tunanin dole zasu bibiyi inda muke?”
“Ta yaya?,na cire duka layukan wayata,sannan koda yayyena da muke uwa daya uba daya basusan inda na nufa ba,tanja……zan iya sadaukar da komai nawa saboda na kubutar da cikin maina……zan iya sadaukar da numfashina dama rayuwarta,JINI NA NE……jinin maina ne” ta fada zuciyarta na tsinkewa,rauni yana son saukar mata don batasan a nahiyar da mainan yake ba,bata kuma san a wacce duniya yake ba a yanzun.
Dai dai sanda saqonta ke sauka ga wayoyin dukkan mutanen dake da muhimmanci a gareta,suka kuma cancanci tayi musu bankwana dai dai lokacin tayoyin motocinta ke shiga qasar KANO. ta zabi kano dinne saboda tasan zaiyi wuya hankali yakai can,asalima ta zabi kano ta zama hanyar fitarta daga nijer da nigeria din gaba daya, saboda batasan kowa ba acan,basu da kowa ballantana a samu fargabar wani da suka sani ya gansu.
Ba bata lokaci tabi cikakken kwatancen da dillalin data kama hayar gidan na sati biyu a hannunsa ya turo mata. Cikin kwanciyar hankali ba tare da kuskure ko batan kai ba sai gasu sun isa qofar gidan dake jerin rukunin gidajen SHARADA NNDC QUATERS.
“Alhamdulillah,alhamdulillah,allahumma inni as’alukal birru wattaqwa” ama ta furta tana zare belt din jikinta sannan ta buda murfin motar tana fita.
Seat din baya ta bude,sultana dake zaune kawai ba tare da sanin ainihin meke faruwa da ita ba ta daga kai suka hada ido da ama. Murmushi ama ta sakar mata
“Sannu daughter,fito mu shiga ciki ki huta” tayi maganar da sakakken murmushi akan fuskarta hadi da miqa mata hannunta. Ba musu ta kama hannun aman ta fito da ita,sai ta miqawa tanja key tana cewa
“Ki bude ku shiga ciki,zan daidaita parking motar sai na biyoku”. A ladabce tanja ta karba,tana gaba sultana dake takawa da qyar tana biye da ita,don bata tana kusan doguwar tafiya irin haka a mota ba. Duk inda zasu muddin yanabda airport to tabbas jirgi zasubi suje su dawo,zata iya cewa wannan shine karon farko data taba shigowa nigeria ta mota.
⚜️⚜️Ya sani har ya kwanta bacci bata shigo dakin ba,to amma yayi tsammanin taras da ita bayan ya farka sallar asuba amma sai yaga lokacinma wayam. Yayi tsammani dukka fushi takeyi dashi akan maganar da Bibi tun ta shekaran jiya,to amma shi ya dauka zata yi masa uzuri,ta dauki bibi a mizanin mahaifiya wadda bazai iya musanta mata ba,saidai yayi mata gyaran kusakuranta cikin hikima idan buqatar hakan ta taso. To a lokaci irin wannan,matsalar sultana da maina matsala ce me matuqar sarqaqiya,dukkaninsu daga maina har sultana babu wani wanda zaiqi a cikinsu,babu kuma wanda bayaso,saidai dole yayi kaffa kaffa game da duk lamarin da ya shafi maina,saboda gudun son zuciya ya shigo ciki,ko kuma duniya tayi masa kallon maras adalci meson kansa da d’ansa,dole ya sanya buqatun sultana da maslaharta a gaba data maina,kodon maraicinta.
Bayan ya gama addu'o'insa ya jawo wayarsa da zummar kiran ama din ya nuna mata kulawa ko yaya ne,ko ba komai ita din uwa ce,itama tana jin yadda kowa yakeji a ransa game da d'ansa,saidai kuma saukar saqon da sunanta saman screen din wayarsa ya katse masa dukka wani hanzari nasa.
amincin Allah ya tabbata a gareka,nayi imani a sanda saqonnan zai riskeka tuni na jima da yi muku nisa ni da d’iyata kuma surukata,inason shaida maka cewa munyi nisa ni da ita domin tseratar da abun farautarku,nisan da banajin nemanku zai iya cimmana,ina rubuta maka wannan saqonne don baka zabi guda biyu……ko ka jirani har na dawo daga balaguron tseratar da rai nayi…..ko ka sawwaqe igiyar aurenka dake kaina idan kaji ba zaka iya zaman jiran hamdiyya ba,ga yarana nan zasu iya kulawa da kansu na sani haqiqa…….ina muku fatan alkhairi……ina kuma fatan saduwarmu ta gaba ta zama da alkhairi,bissalam.
Hannunsa ya sanya ya sharce gumin dake goshinsa yana jin wani tashin hankali yana sauko masa. Babu MAINA babu HAMDIYYA sannan kuma babu SULTANA gaba daya,duka cikin wat uku kacal?,wannan wacce irin jarabawa ce haka ke tunkararsu?,wacce irin musiba ce haka?. Kaman an mintsini aba sai ya miqe cikin hanzari,ko slippers din qafarsa bai maida ba cikin sassarfa ya nufi sashen ama.
Loko da saqo na cikin sassan ya fara bincikewa kamar wani zautacce,kaf ya karade sannan ya koma kewayen gidan ba ama ba dalilinta,sai ya sake komawa bedroom dinta a nan yaga shaida. Ta kwashe duk wani abu nata me muhimmanci kamar yadda maina yayi. Haka dakin sultana an kwashe kusan komai nata me muhimmanci,a farfajiyar gidan kuma da ya duba yaga babu motarta guda daya,a nan ya saddaqar da cewa lallai abinda ta fada din da gaske ne.
Bai tsaya duba qarfe nawa ba a sannan ya soma dokawa abdulhakeem kira. Da alama yana kusa da wayar,don bugu daya ya dauka. Abirkice aba ke tambayarsa hamdiyya ta iso?.
“Ta iso ina?” Ya tambayeshi cikin daurewar kai
“Don Allah idan ta iso kada ku bata dama ta sake fita ko ina”
“Akan me kake magana ne hamidou?,ina hamdiyya din tace zata je?,ina cewa ko jiya munyi waya tana nan nijer,bata kuma cemin zata zo Nigeria ba” komawa da baya aba yayi ya zauna,sannan ya warwarewa abdulhakeem komai.
Shi dinma ya rude,don har yanzu ana ju da auta,wanann gatan da soyayyar ba inda suka je,musamman mutuwar iyayensu ya sanya sun sake dora mata gata
“Kada ka damu aba,muddin tana cikin Nigeria dinnan ba zata fita ko ina ba,zamu dubata kuma zamu tabbatar ta dawo dakinta” abdulhakeem ya fadi cikin fargaba xa kaduwa,duk da yana boye hakan a zahiri gudun sake jefa aba cikin wata damuwar.
Ya jima zaune a wajen,baisan ta yaya zai tunkari bibi yace mata ama ta dauke sultana ba, ba'a san kuma ina suke ba,ina suka dosa?,sanda kuma zasu dawo din kwanaki ne da suka tasamma watanni sha biyu qila harda doriya.
Yana wannan tunanin sai ga Omar kamar an jefoshi,wayarsa a hannu,ya tsaya gaban aba yana miqa masa Wayar. Hannu ya sanya ya karba yana dubawa. Saqo ne dai daga hamdiyya tana dora ma Omar din alhakin yiwa bibi bayani
“Ka gaya mata Omar ta kwantar da hankalinta,nayi alqawarin dawo mata da sultana cikin aminci” wannan shine statement dinta na qarshe………
⚜️Komai akwai cikin gidan,kusan ba abinda suka shiga dashi sai kayan sawarsu da ba wani masu yawa ba,sai kuma kayan abincin gida da tayi order ta wani app suka iso gidan babu dadewa suka dire mata komai.
Sai bayan magariba ta nutsu,wunin ranar suna dan gyare gyare cikin gidan ita da tanja,sultana na baccin gajiya,zuwa magariba din har abincin dare tanja tayi,bayan sallar isha'i dukkansu suka hadu cikin madaidaicin falon da duka duka baifi girman toilet din ama ba nacan nijer da kuma gidanta na nan dake abuja ma.
Zuwa magariba tanja da ama sun kintsa gidan tsaf,duk kuwa da cewa bawai zama zasuyi ba gaba zasu qara nan da wasu 'yan kwanaki amma ama ta tanadi komai da zasu buqata a kwanakin,ciki harda abincin ci ruwan sha da drinks.
Zuwa magariba har girkin dare tanja ta gama. Ama na gama sallar magariba din ta fito falon tana cewa tanja
“Shiga ki duba sultana,tun yamma data kwanta banji motsinta ba” ta fadi tana zama saman kujerar falon hadi da kunna tv plasma din dake zaune saman TV stand.
Bata da wata sanayya da gidajen tv sosai,don ba ma'abociyar kallo bace,don haka tabar tv din saman channel din dake haska labarai a dai dai lokacin.
Bata gama maida numfashinta ba tanja ta fito a dan rude
“Hajiya zazzabi ne ya saukarwa sultana fa,kuma irin me zafinnan da likita yayi magana akai” ajjiye wayar hannunta da zuwa yanzu ta sauya layi zuwa na Nigeria,shima temporary ne,don dole tana da buqatarsa wajen neman visa dinsu da kammala komai na tafiyarsu,uwa uba kuma ita din ma’abociyar hawa social media ne duba labaran kasuwanci da sauran al’amuran da suka shafi rayuwa
“Subhanallah,ya salam,muje na gani” ama din ta fada hankalinta yana dan daguwa.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 20
Riris ta sami jikin nata,dole ta soma laluben asibiti dake kusa da GRA din ta hanyar taimakon MAP. Allah ya taimaketa ta samu wani private hospital nan kusa dasu wanda ko a qafa ma kana iya takawa.
Ta sani dama babu makawa,qarin ruwa ne dole shi za'a mata,saboda irin wannan zazzabin gaba daya sanyawa yake lokaci daya ruwan jikinta yayi qasa. Nan gabanta suka kwana, tausayin sultanan yana ratsa ama. Ta hadu da azababben laulayi me zafi,bata sani ba ko harda quruciya a ciki?.
Cikin taimakon Allah washegari taji qwarin jikinta sukayo gida.
Sai yamma sannan suka zauna cin abinci. Cakula abincin kawai takeyi,hankalin ama duka yana kanta. Ta yaya wannan dan tayin dake manne da ita zai zama yadda akeso?,bayan kwata kwata bata wani iya cin abinci?,duk irin lokacin da ama ke kashewa tayi mata nau'ikan abinci kala kala. Bata taba damuwa da bata lokacin da takeyi ba,duk da aba kadai take kashewa lokacinta a kitchen,aah.....damuwarta na rashin cin abincin sultana dinne.
Afakaice bayan rashin cin abincin ta karanci kamar akwai damuwa boye qarqashin zuciyarta,don haka ta kirayi sunanta a hankali. Kai ta daga tana kallon ama da zugaggun idanunta da a yanzun kullum a kode suke tasss kamar danyen nama
“Banason ganin wannan damuwar sultana,zan cika miki alqawarinki……zan maidaki wajen bibinki,zan kuma karbi ko meye kika haifa,idan kinso kice ma ba kece mamarsa ba dukka na yarda……amma muddin kina son hakan ta kasance sultana sai kina sakin jiki kina cin abinci” wasu hawaye ne masu sanyi suka gangaro daga idanunta
“Basa ciyuwa abincin ama…….sai naji ko kallonsa bana sonyi,bazan iya ci ba amma yadda kikeso” sake sassauta murya ama tayi
“Shikenan,calme-toi(kwantar da hankalinki),ba lallai bane sai kinci duk abinda aka dafa din ba…..duk sanda kikaji akwai abinda kike sha’awar kici to komai rana kome dare ki gayamin ko ki gayawa tanja,zamu tabbatar an dafashi kinji?” Kai ta gyada mata a sanyaye
“Yauwa,madalla……yanzu wacce qasa kikeso mu wuce?,don banaso mukai sati uku a nan,inason na kaiki inda za’a kula dake,ba zaki sha wahala ba” har qasan ranta taji danji sanyi ya saukar mata,abinda zata iya cewa ta jima rabon da ta jishi. Ta dan lumshe idanunta tana jin yadda zuciyarta ta gamsu da tayi nesa da NIJER qwarai da gaske,tayi nesa da qawayenta dama idanun da suka santa,tayi nesa da dukkan cakwakiya,a yanzu idan ka debe bibi da aba bata qaunar ganin duk mutumin da ta sanshi a baya,tanaso ta nesanta kanta da kowa,da da halima zataso ta rayu ita kadai
“Wacce qasa kikeso?” Ama ta datsi tunaninta tana sake tambayarta. Abaya dukkan burinta shine aba ya kaita France,kullum zancanta kenan,har yana tsokanarta
“Tunda kikaje makka kikaje madeena aikin gama yawo sultanan bibi…..amma itama France din zan kaiki,amma fa sai ranar da kika gama école secondaire(secondary school),naga kuma résultat(sakamako)nki yayi kyau,zan hadaki da ama idan an dace zata shiga ta can ku tafi tare har sai kin gaji sannan ki dawo”.
A wannan karon sai taji kamar an zare qasar fit daga zuciyarta,maimakon ta cewa ama itace zabinta sai ta buda baki a hankali tace
“Austria”
“Austria?” Ama ta sake tambaya,don itama France ta tsammaci zata ce. Kai ta gyadawa ama din tana me tabbatar mata,sai ama din ta sauke ajiyar zuciya tana cewa
“Très bien(ba laifi)” sai ta jawo wayarta ta kunna data ta soma danne danne.
*Sati biyun da sukayi cikin garin kano sunyi shine cikin gida ba tare da zuwa ko ina ba,idan ka gansu sun fita din to tabbas zasu miqa sultana ne asibiti. Sultanan da ko yaushe jikinta ke qara zafi da rikicewa.
Wani irin bahagon laulayi takeyi mai bala'in zafi da wahala. Duk yadda ama tayi shekaru a duniya,taga kuma masu ciki kala kala,itama kuma tayi kalar nata cikin har sau uku ta jima bataga masifaffen laulayi irin na sultana ba. Sosai take a galabaice,bata iya komai sai kwanciya,sai kuma kuka daya zame mata tamkar sallolin farilla guda biyar.
Kullum gari ya waye rana ta fito bawa kanta mutuwa takeyi,azabar da takeji a kowacce gaba ta jikinta tana jin ba irin nau'in azabar da zakaji ka rayu bane. Ta sake zama 'yar firit da ita,sai wani mahaukacin haske da tayi,idanunta suka sake fitowa tare da yin wani irin haske me sheqi. Saidai kuma duk yawan gashin nan nata da sumar nan babu su,yanzun haka qaramin ribbon ya isa ya riqe 'yar sumar dake kanta. Bata um bata um um,kuka a yanzun ya fiye mata komai cikin rayuwarta.
Yanayin sultana din ya sake cirewa ama nutsuwa,tausayinta takeji kamar kamar me,inda tana da iko da kuma me yiwuwa ne da tuni ta fidda cikin daga jikinta ta dawo dashi nata jikin ko zata samu hutu koda na kwana daya ne tak.
AUSTRIA
VIENNA
VIENNA INTERNATIONAL AIRPORT (flughafen whien_schwechat VIE)
A nutse suke saukowa daga jirgin Ethiopian airlines wanda yayi jigilarsu daga kano ta dabo suka yada zango a Addis ababa,daga addis ababa din suka sauka London,daga london kai tsaye zuwa Austria babban birnin Austria din wato Vienna.
Hannun sultanan wadda tayi wani dan qaramin kyau cikin wasu skirt and blouse da suka dace da jiki da kalar fatarta,sai headscarf data nannade kanta dashi,wanda hakan ya bayyana fuskarta data bayyanar da rama quru quru.
Backpack bag ne a kafadarta guda daya, sauran duka luggage dinsu yana hannun tanja. Shima ita ta dage kan zata iya amma aman hanata tayi.
Hannunta cikin na aman,wadda ke saye da wata doguwar riga me rubi biyu beig color saqar qasan oman,sai rufaffen takalmi data saye qafarta dashi. Qwayar idanunta lullube da wani sun glasses baqi da ya qara mata kwarjini ainun. Kana kallonta kaga classy maama,muddin baka santa ba ba zaka taba tsammanin ita ta haifi saurayi haka kaman aliyyu ba, zakayi tunanin almu shine yaronta na fari. Tana da kyan jiki,tana da son ado,idan akace ado ado me aji wanda bai fiya daga hankali ba,irin adon da duk wanda ya kalla zao burgeshi ya kuma ga cewan ya dace da age dinta.
Duk da ba kasafai ta fiya zuwa Austria ba,to amma abune na aiki da ilimi,don haka tun kafin su tsoma qafarsu cikin qasar hatta da inda zasu zauna tsahon wadannan watannin ta gama dashi,don haka suna sauka taxi suka dauka kai tsaye suka wuce masaukinsu.
SECOND DISTRICT Leopoldsdadt
Unguwace dake da wani irin tsari me kyau tare da saukar da nutsuwa, nutsuwar da tunda suka shigo unguwar har qasan rai da zuciyar sultana taji yanayin unguwar yayi mata. Suna da wasu irin jerarru kuma tsararrun Street da aka cikasu da bishiyu dake bada wadatacciyar iska da inuwa me kwantar da hankali.
A nutse suka isa second floor,inda anan apartment nasu yake. Babban falo ne yalwatacce dake dauke da dining area,budadden kitchen,balcony daga gaban gininsu da zai baka daman samun iska me kyau da ganin yanayin ginin unguwar,sai dakunan bacci guda uku madaidaita dake manne da toilet kowannensu. Yanayin ginin gini ne me matuqar tsari wanda ama tayi amanna zai dace da tsarinsu,komai an zuba,hatta da kayan abinci basu da abinda zasu buqata.
Tun daga daren har zuwa wayewar gari ama bata zauna ba. Kwanaki biyu tayi a tsaye,sai data tabbatar duk wani da zai zamewa rayuwarsu tilas na su nemeshi ta gama da matsalarsa a tsahon shekara guda da take sanya rai zasu kwashe a qasar. Tun daga booking na asibitin da sultana zata dinga zuwa anti natal,tayi mata register da wani center na bawa mata masu juna biyu kulawa da kuma shawarwari,ta sake mata register da cikakken likitan dake lura da matsaloli da qwaqwalwa kamansu depression anxiety da sauransu. Center ce me kyau data jima tana bin qwaqwafi da bincike a kanta,tanason duk wani damuwa ya gushe daga zuciyar sultana din,tana sha’awar taga sultana ta fuskanci rayuwa da kyau,tanaso ta haihu successful ba wani matsala da zata shafeta ko ta shafi abinda ke cikinta. Ta canza layukan wayarta,ta kuma canza dukka accounts nata da take amfani dasu,kama daga Facebook page dinta,instagram dinta da watsapp dinta,daga ita har sultana suna buqatar nutsuwa,suna da buqatar su manta da kowa da komai na wani dan lokaci.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 21
Hutun sati guda kacal sukayi duk wani abu data biyawa sultana din tayi qoqari taga ta fara zuwa. Duk da zuwan nata sai ya zamana asha ruwan tsuntsaye saboda yanayin jikinta na yau lafiya gobe babu.
Cikin nasara da taimakon Allah sannu sannu tana zuwa ganin likitanta sai aka fara samun sassauci,don an samu ci gaba tayi katari da irin abincin da takeso a wata fita da ama tayi dasu cikin unguwarsu. Street food ne da sukeyi a wani kebantaccen waje,ama din bata taba tsammanin sultana zata iya cin abincin ba,don har ta kira waitress tace a maida,sai ta buda baki da muryar nan tata data zama sasaanya tace
“Ama ni zanci” a mamakance take kallonta,cikin harshen German tace su ajjiye. Kaman wasa ta koma da baya ta zubawa sultanan idanu,sannu sannu sai gashi ta tashi dashi. Abun ya yiwa ama dadi,sai suka maida wajen gurin zuwansu duk dare,don acan ne kadai sultanan ke iya ci ta qoshi,koda zataci tayi amai,amma tanaso,hakanan ana samun wani yana zama a cikinta.
Kaman yadda taci burin sadaukar da komai nata ta sadaukar din,don lokutta da yawa tanja na girmama girman qaunar data karanci ama na yiwa cikin dake manne jikin sultana,ko kadan batajin kudin dake fita a jikinta,duk da cewa ita din ahalin abunne,ta tara da yawa an kuma tara mata,amma saidai daga qasar har zuwa unguwar da suke zaune din tana cikin nau'in gurare masu tsadar rayuwa a duniya,amma tanja bataga alamun hakan sam sam yana damun ama ba.
Sannu sannu suka kwashe watanni uku a Austria......daidai watannin cikin sultana shida cif,ba labarin gida a kunnuwansu kamar yadda gida basusan wacce duniya AMA TANJA DA SULTANA suke ba.....bare maina da tun daga wancan ranar ko me kama dashi basu sake gani ba,basu sake jin komai da yayi kamanceceniya dashi ba..... tun uncle abdulhakeem suna cigiya har gwiwoyinsu ya sare.......tun suna cigiyar maina kadai har suka koma hadawa da cigiyar ama......tun hankalin aba bai tashi da yawa ba,yana ganin kamar adadin Tex naban haqurin da yake tura mata yana riskarta......girman soyayyar dake tsakaninsu zata hanata yin nisan zango.......zata kuma waiwayeshi.....har ya sare ya fara tunanin ta ina zai nemo hamdiyya?,ta yaya zai maidowa da bibi farincikinta?. Duk wani kuzari da walwala na family din MAYAK'I yayi nasa guri sai abinda ba'a rasa ba. BA MAINA BA AMA BA SULTANA wadannan abubuwa dasu suke kwana kuma dasu suke tashi cikin zuciyar duk wani ahalin mayak'i.
****K’arfe takwas na dare agogon qasar Austria,daidai lokacin da ama ke tsaye gaban cupboard din sultana tana zaqulo mata kaya.
A qalla kayan dake zube saman madaidaicin gadon sultana din sun kusa kala ashirin,saidai kowanne a ciki sultanan ta gaya mata baya shigarta.
Daga qarshe hannunta ya damqo wata free size gown,golden brown ce da ratsin baqi,ama ta dagata tana kallonta hadi da sauke ajiyar zuciya.
K'ofar toilet din dakince ta bude,sultana ke takowa a hankali daure da babban towel.
Idan a watanni biyun baya kaga sultana a yanzun zaka iya rantsewa ba ita bace,ko kuma kace
“Wanne irin ci takewa abinci haka?” Zaka kuma iya qaryata duk mutumin da yace maka baqar wahala takesha,bata iya bacci da dare sosai,bayan dukka ‘yan kwanaki sai ta ziyarci likita ya qarawa jijiyoyinta ruwa.
Kamanninta tun daga jikinta zuwa fuskarta sun dauki hanyar bacewa. Tana takowa gaban ama ama din na kallon idanunta
“Kuka kikayi cikin bandaki sultana?” Ta jefa mata tambayar data sanya sultana ala dole kauda kanta. Kukan tayi,kukan data kwan biyu batayi irinsa ba saboda rashin qwarin jikinta. Fuskarta ta kalla taga yadda ta koma,gaba daya kaman ba sultanan bibi ba?,me yasa ama ta tilastata akan tabar cikinnan?,me yasa bata yarda da shawarar bibi ba?,kullum rana ji takeyi kamar ruhinta zai fita daga gangar jikinta,wani lokaci ma sai taji numfashi kamar na mata wahalar shaqa,wani abu ya yiwa cikinta qabe qabe,yayita mata motsi kuma yana dukan bangon cikinta,wani lokaci ta tashi ta zauna a firgice cikin dare,wani lokaci ta dafe gurin ta saki kuka me tsuma zuciya.
Tunda uwarta ta haifeta bata taba jin ana motsi cikin mutum ba,a ranar data fara ji din kusan haukacewa ama tayi da kuka da firgici. Ita sa tanja sai da suka kusa kwashe awa guda suna mata bayani suka kuma kwatanta mata kafin su samu ta sassauta,saidai har yau idan cikin zai motsa to yana motsawa ne da wani irin miki a zuciyarta.
Ganin tayi namijin shanye damuwarta sai ama din bata kuma tuhumarta ba,ta zauna tana miqa mata kaya tana shiryawa. Gaba daya girman cikin ba zakace na haihuwar fari bane,bayan haihuwar fari ma ace cikin yarinya kaman sultana?. Duk da a yanzun wani girman dole yazo mata,ta cika ta zama mace,amma idan ka qare mata kallo tsaf idan kana da nazari zakazan yarinya ce danya shataf.
Ko a jiya sai da sukayi zancan girman cikin da tanja
“Next month zamu koma ganin likita,zan masa complain naji me zaice” ama ta cewa da tanja
“Amma hajiya anya baki tunanin tagwaye ne a cikin nan na sultana?” Sai da gaban ama ya fadi
“Tagwaye a cikin sultana kuma?,ina zata kaisu?” Ta tambaya da fargaba,sai kawai tanja tayi murmushi
“Shikenan,Allah dai ya raba lafiya kawai zamuce cikin amincinsa”
“Allahumma ameen” ama ta amsawa tanja,saidai cikin ranta tana nazarin maganganun tanja din
A nutse ta gama shirinta tsaf sannan ama ta sanyata a gaba suka fito. Yau din tanja tace zata zauna cikin gida,ita ta soma gajiya da kallon masu jajayen fatar nan. Sosai maganar ta bawa ama dariya,sultana kuwa murmusawa tayi qasan zuciyarta ba tare da fuskarta ta nuna ba.
Hakan kaman qa'ida ya zamewa ama tun sanda likitan ya basu shawarar fita strolling da sultana din saboda sake samun qarin lafiya da kuma gujewa qaruwar hauhawar jininta. Tare suka jero ta layin unguwar da yafi kama da titi sabooda shimfidaddiyar kwalta data maye gurbin qasa da mu muke fama dasu cikin layukanmu. Idan ka hangesu daga nesa zakayi tunanin yaya ce da qanwarta,idan suka kusance ka kuma sai kaga UWA da 'YA sak.
Yau din shuru ne ya soma ratsa tafiyar tasu,har sai da ama tayi gyaran murya
“Yau bakison kowanne labari ne?” Ta fadi tana dan satar kallon sultana,wadda tun sanda ta fara zuwa center din data mata register ake samun sauqin wasu abubuwan,koda ba zaka ganta tana dariya ba amma a qalla akwai raguwar dakuwa kaso sittin cikin saba’in data dawwamarwa fuskarta,to amma yau din da alama akwai wani abu da ya taba zuciyarta
“Inaso” ta fadi a taqaice,sai ama ta dage dukka kafadunta
“Shikenan,zan baki labarin qasar Germany,sanda mukaje da abbana duka duka shekaruna goma sha hudu……amma saikin gayamin meye yake damunki,karki manta……munyi alqawari dake kin daina boyemin komai” ama ta fada taba nuna fuskar sultanan da dan yatsa.
Duk yadda taso jurewa saida hawaye suka taru a idonta,tasa bayan hannunta ta matsesu sannan bakinta yana dan rawa tace
“Na gaji da cikin ama,don Allah yaushe zai baki na huta?” Tausayi da dariya dukka suka kama ama din,amma tausayin ya rinjayi dariyar. Tsabar sangarta da gata batasan ma wata nawa ne ciki yakeyi a jikin mace ba kafin ta haihu,tsabar qanqantar shekarunta ma batasan yadda zatace Mata yaushe zata haihu ba,sai ta kama hannunta suna dab da wani shop na Shan coffee da snacks don haka suka qarasa. Kujera taja mata ta kalleta,ko batayi magana ba tasan me take nufi,don haka sai tayi taku biyu,ta isa gaban kujerar ta zauna,fararen idanun nan a narke.
Murmushi ama din ta sakar mata,ta daga mata yatsanta guda sannan ta shiga shop din. Da kallo sultana ta bita harta bace cikin shop din,sai ta zuqi numfashi wanda yakai mata har tsakiyar hunhunta. Da sauri tare kuma da wani irin gaggawa ta saki numfashin hadi da fesar dashi waje tana zare idanunta.
Cikin kowacce kafa ta numfashita.....cikin kowanne sasanni na shiga da fitar numfashinta qamshin yakai. Qamshin da tafi tsana a duniya,qamshin da batajin ko da tana kwance ne a kushewarta muddin qamshin zai gitta ta gurin zata iya jiyoshi,qamshin da jikin mutum daya ta sanshi,ta kuma yi masa mummunar hadda me wuyar mantawa a baqar ranar da tayi silar jirkita dukka farinciki walwala da tarin mafarkan data tanadarwa rayuwarta.
Tsam ta miqe tsaye dukka jikinta yana rawa,ta ware idanunta tana duban kowanne sashe na wajen. Ba kowa,bata ga kuma kowa ba,hasalima kaf wajen kamar ita daya ce baqar fata,sai kuma ama data shiga ciki.
Dafa kafadarta taji anyi,abinda ya sanyata wani irin bahaguwar juyowa,sai idanunta ya fada cikin na ama. Kallon kallo suka tsaya yiwa juna,ama tana kallonta cikin mamakin abinda ya firgitata daga shiga ta fito bayan wajen safe yake,yayin da ita kuma razanar da tayi da kuma tuna mata da mummunar ranar da sanadiyyar wanzuwar qamshin ya haifar mata ya sanya zuciyarta raurawa,kawai saita aza fuskarta saman kafadar ama ta saki siririn kuka.
Tasan dama akwai sauran qunci cikin zuciyarta,wanda babu wata hanya da zata samu sassaucinsa saita hanyar kukan,don haka batace komai da ita ba,ta jata jikinta sosai tana bubbuga bayanta,har sai data nutsu don kanta sannan ama din ta maidata saman kujerarta,ta kuma tura mata daya daga cikin nau'in abin shan da shima akan dace ya zaunawa cikinta.
Bata tambayeta ba hakanan batace mata komai ba sai da taga tana diba da kadan da kadan kamar me ciwon baki tana sha sannan ama din tayi gyaran murya tana gyara zamanta
“Next month zamu koma asibiti,zan tambayeshi wacce rana ne zaki haihu,zakiji in sha Allah,amma kinsan zai iya ce miki ba yanzu ba?” Da sauri ta daga kai tana wulqa idanu,idanun nata cikin na ama, fuskarta ta narke sosai cikin nuna zallar fargaba. Sai ama ta dage mata dukkan girarta
“Eh mana,ya hana wannan koke koken,sannan yace ki dinga daurewa kina cin abinci sosai haka ne?” Kai ta gyada mata a hankali
“To me kike tunanin zai faru idan mukaje ya gwadaki yaga babyn baiyi girman da zaki haihu ba?”
“Zanci ama,don Allah kice masa kada yacemin ba yanzu ba,bana iya bacci ama,bana iya komai,dukana kawai yakeyi a ciki na,kullum dare a zaune nake…..” Ta qarasa fada tana saka tafin hannunta guda tana share sabbin hawayen dake sauko mata. Tsananin tausayinta sai da ya sanya ama din taji qwalla sun sauko mata amma ta daukesu cikin dabara,saita miqa hannu tana dan bubbuga bayanta cikin dabara.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 22
Ganin ta zage tasha abun sosai sai ama ta yanke shawarar su qara nisan zango a tafiyarsu don ya saukar mata sosai,kada su koma gida da wuri ya dameta ko ya sanyata amai.
Cikin salon jan hankali ama ke bata labarin Germany,har zuwa sanda sukazo giftawa ta wani baby shop. Har sun gota amma ta tsaya,sai a sannan ta tuna babu koda qyallem handkerchief da ta siya da sunan kayan haihuwa. Juyawa tayi ta dubi sultana
“Mu shiga nan ki jirani nayi siyayya” bata musa ba ta sanya kai tana biye da ama din.
Guri ta sanya ma'aikatan gurin suka bawa sultanan tace tayi zamanta,gudun kada tace tazo ta tayata zabe taje ta jangwalowa kanta,qilu ta jawo bau.
Sosai ta nutsa cikin shagon,ta dinga zaben kaya designers masu tada da sukaja pounds sosai. Samun kanta tayi da daukar duk abinda ya bata sha'awa,musamman kayan baby girl.
Har yanzu akwai wannan qawa zucin a jikinta da kuma zuciyarta,har yanzu tanason baby girls,don dai kawai lokacin haihuwarta ta fuskanci ya wuce ne.
Sanda ta shiga bangaren overalls 'yan ubansu,saita tsinci kanta da zaben komai pink,haka kawai cikin zuciyarta taji tana da burin inama ace babyn ya zama mace?, murmushi ya subuce mata ba tare data shiryawa hakan ba.
Daidai bangaren teddies ama ta ajeta. A nutse takebin wajen daki daki da kallo,komai na wajen me kyau ne,alamu dake nuna cewa komai na cikin shagon zaiyi tsada kenan.
A hankali wani tsohon emotion nata ya fara taso mata. Nini dinta ta fado mata wadda har kwanan gobe batasan inda tayi ba. Allah ya zuba mata qaunar teddy,duk da wannan emotion din nata yaso mutuwa murus daga gangar jiki harma da ruhinta.
Har ta zare idanunta daga kansu sai hankalinta ya fusgo mata wata kyakkyawar pink teddy. Maida dubanta tayi,ta miqa hannunta tana shafata. Sosai jikin teddy din yayi mata,haka ma fasalin da akayi mata
“Ki dauka idan tayi miki” ta tsinci muryar ama daga bayanta. Da sauri ta waiwaya ta kalli ama dake riqe da wani babban kwando da ta cikashi taf da suturu,saita maida dubanta ga fuskar ama din tana girgiza kai alamun a’ah,sannan ta miqe a hankali da zummar barin wajen. Da kallo ama ta rakata sai kawai ita ta saka hannu ta zaro teddy din ta jefata a kwandon kayan. Har tayi gaba ta dawo da baya,ta zake zabar wasu guda biyar suka zama shida cif,sannan ta wuce wajen lissafi.
Mamaki ne kawai ya kashe sultana sanda taga uban kayan da ama ta diba,ashe kwandon hannunta na daxun sauran kayanne kawai. Kamar ba da guminta take neman kudin ba,ta zare Pounds masu ciwo ta biya kudin kayan tas,sanann ta bada Adress din inda za'a kai mata suka fice abinsu daga shagon.
Har ranta bataji komai ba,jinin maina ne kuma tsatsonta itama.......inda ana kyautar rai tabbas zata iya sadaukarma ahalinta,xata iya komai domin jininta,ita a yanzun ma da kwanakin cikin ke qara nisa sai takejin zumudi qauna da kuma soyayyar abinda ke cikin na sake kamata,taji ta dokanta da son ganin abinda ke cikin sultana din,ta matsu ya iso duniya.
****Sake duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta ama tayi,mamaki ya sake kamata,me sultana din keyi shuru bata fito ba har yanzu?,bayan tasan inda zasuje din da kuma muhimmancin wajen.
Kamar ta aika tanja sai kuma ta fasa,ta miqe tana ajjiye medium veil din hannunta mahadin doguwar rigar jikinta ta gyara zaman agogon hannun nata tana wucewa dakin sultanan.
Zaune ta sameta saman stool a gaban madubi,daure take da babban farin towel,sumar kanta na nannade tsakiyar kanta. Tuni ta jima da zama qazama ta wannan fannin,bata yarda da abinda zaya taba mata kanta duk qanqantarsa,sai ama tayi da gasken gaske sannan ake wankeshi a kuma maidashi yadda yake.
A nutse tare da sallama ama ta shiga dakin,waiwayowa sultana din tayi,hawaye ne shabe shabe kwance a fuskar tata
“Ya salam” ama ta furta qasa qasa. Itadai tunda take bata taba ganin mutumin da kuka baya damunsa ba baya kuma yi masa wuya ba irin sultanar
“Yanzun kuma kukan meye?” Ta tambayeta tana isa bayanta ta tsaya tana duban fuskarta cikin mudubi. Cikinta ta kalla,sai a sannan idanun ama yakai kai,ta yaye towel din dake jikinta,sai turtsetsen cikin a gaba kai kace saura satittika ta haihu
“Menene?” Ama ta sake tambayarta cikin fargabar kada ta bata amsar wani abu ne ya samu cikin
“Fasamin ciki zaiyi ama……sai dukana yakeyi nan da nan” ta bata amsar tana rushewa da kuka tare da nuna mata gefe da gefen cikinta da yatsanta. Ga dariya ga kuma tausayi,da gasken gaske sultana danya ce shataf,babu wani abu data sani dangane da ciki ko haihuwa,uwa uba auta kuma ‘yar fari,wautar tata tayi yawa.
Gaban sultana din ama ta zauna tana qoqarin fahimtar da ita cewa alama ce ta lafiyar abinda yake cikinta
“Ni na tambayeshi yana lafiya?,ya mutu mana” ta fada tana buntsuro baki gaba
“Subhanallahi” ama ta fadi tana zaro idanu,don sosai maganar ta daketa, jikinta yayi wani mugun sanyi,tsoro kuma ya shigeta. Kada dai ace zuciyarta ta taso da qeqashewa da qiyayyar abinda zata haifa din kamar yadda ta yiwa mahaifinsa muguwar tsana?. Wannan tunanin kadai ya sanya zuciyarta rawa,bata fatan kuma wannan ya zama qaddararta ta gaba,batasan yadda zata fuskaci wannan qaddarar ba kuma
“Sultana?” Ta kirayeta a sanyaye tana kallon tsakiyar qwayar idanunta. Duban aman tayi amma sai ta janye kallonta daga kanta,karon farko da taji wani nauyi na aman,taji kuma nauyin kallon idanun aman,jikinta itama ya sanyaya,taji a jikinta kamar ta furta wani abu da ba dai dai ba.
“Kinaso muyi fada dake?” Ta sake tambayarta with seriousness. Da sauri ta girgiza kai tana jin zuciyarta tana karyewa
“To kada ki sake fada,kada na sake jin kinyi wannan furucin,akan kowa ma bare d’an cikinki,da yake kwana ya tashi a jikinki,bashi da wata uwa sai ke,ke kadai kika dauki cikinsa kikasan wahalarsa,mu nan dukka tayaki kawai mukeyi kinji ko?” Kai ta jinjinawa aman,sai tayi saurin kauda zancan ta hanyar cewa
“Oya…..tashi ki qarasa shiryawa,idan munje wajen likita saiki kai masa qararsa,zai masa fada nasan,zai daina kuma dukanki” wannan ‘yar maganar ta sanyayawa sultana rai,ta kuma miqe din ta shirya tsaf a gaban ama din kamar yadda ta saba shiryawar,ba wani nauyi ko kunya ko digo da takeji nata.
Yauma sai da sukayi tattaki subway,sannan suka hau train zuwa asibitin.
Dr abdur'razaq mansoor,cikakken likita dan asalin qasar Egypt shine likitan dake duba sultana,likita ne me matuqar kirki da kula da addini,yana da tausayi da kulawa sosai. Tun ranar farko da ya fara ganin sultanan tausayinta ya cikashi,ya fahimci yarinya ce qarama sosai da bata gama sanin rayuwa ba.
Yanayin nutsuwar likitan da tausayin da ya gwada ma sultanan ya sanya ama bata boye masa komai ba
“Zan bata kulawa in sha Allah,zata haihu kuma lafiya” a boye ya baiwa ama addu’o’in da zata dinga tofawa sultana din a ruwa,kuma ko sau daya aman batayi fashin tofa mata din ba ba tare da sultana ta sani ba. Duk wani gorar ruwa na gidan da tasan sultanan zata iya sha sai data budesu ta tofa din,daya daga cikin sirrikan abinda ya kawowa zuciyarta nutsuwa ya kuma sake tanqwara ta ya sanya mata dangana.
A irin qasashe dake da ci gaba irin haka,zaiyi wuya kaje ganin likita ka samu cinkoson marasa lafiya suna jiran likita,hasalima lokuta da dama saidai ka samu likitan yana zaune kawai yana hutawa ko wani research da ya danganceshi. Don haka mace daya ce ta fito number dinsu tayi appearing jikin board na office dinsa don haka suka wuce ciki kai tsaye.
Da fara'arshi da kuma sakin fuska ya musu maraba. Ya saba sam sultana bata magana har su gama ganinsa su tafi,amma hakan baya hanashi dan tsokanarta janta da wasa kadan don ta saki jiki da kuma tambayarta yanayin lafiyarta.
Sai da ya gama mata dukka tambayoyin da aka saba,ya nemi jin ko akwai wata matsala da take fuskanta?. Murmushi ama tayi sannan cikin harshen France don sultana din taji ta gaya masa
“Tace dukanta cikin yakeyi,ta gaji dashi yaushe zan karba?” Qaramar dariya Dr abdur’razaq mansoor ya saki
“Yau zamu duba muga me yake faruwa sai a gaya masa ya fito haka momy ta gaji” shi da ama suka dan saki dariya,banda sultanan da take binsu kawai da kallo.
Komai ya hada sannan ya bata umarnin hawa gadon scanning. Karon farko da za'a yi mata scanning din tun bayan wanzuwar cikin.
Kusan daskarewa Dr abdur'razaq mansoor yayi yana ci gaba da yawo da na'urar saman cikinta
“Subhanallah” kawai yake furtawa lokaci lokaci idanunsa qur bisa allon computer din.
Subhanallah din da yake fada ta sanyawa ama fargaba,amma ita dinma saita dinga ambaton sunan Allahn kawai,don tunda taji baice komai ba qila babu buqatar yin maganar gaban sultana.
Yana kammalawa ya danna wani madanni na kiran nurse,ba jimawa nurse din ta shigo,cikakkiyar baturiyar Austria,saidai ita dimma da alama macace me kirki da yawan fara'a.
Cikin harshen German yace da ita ta kaita garden na masu juna biyu,sannan ya sake juya harshen nasa cikin yaren France ya yima sultanan magana. Ba musu ta miqe ta saki doguwar rigarta,ta kuma gyara yafen mayafin nata tabi bayan matar.
Da idanu ya bisu,sai daya tabbatar da fitarsu sannan ya dawo da dubansa ga ama wadda ta tsurawa hoton scanning din dake jikin allon computer din idanu,kwanyarta nason rarrabe mata gaskiyar abinda idanunta ke gane mata.
Hannu kawai ya miqa ya juyo mata da fuskar computer sosai yana kallon idanunta,cikin yaren faransanci yace mata
“Ina tayaku murnan samun ‘yan biyu,yarinyarki tagwaye ne a cikinta kamar yadda na jima ina zato” maganar tazo mata a mugun ba zata,cikin hanzari ta maida dubanta ga Dr abdur’razaq. Ya fahimci she was shocked,sai yayi murmushin nan nasa yana dora dukka hannuwansa kan computer din.
Kai tsaye ya canza hoton da take gani zuwa 3D scanner,take fuskokin yaran dake kwance cikin mahaifar sultana din suka bayyana tarwai.
Ko ina a jikinta ya dauki rawa,ta sanya hannuwanta dukka biyun tana rufe bakinta,bakin nata dakeson kama sunan Allah amma rawar da yakeyi ya sanya ta kasa,Dr abdur'razaq bai waiwayo ya dubeta ba yaci gaba da mata zooming fuskokin guda biyu da suka zama cikakkiyar fuskar bil'adama,fuskokin da suka cika suka kuma bayyanar da kamanninsu,suna rungume da junansu
“Bacci sukeyi,inda idanunsu biyu zaki iya ganin motsawar kowannensu,kukansu ko walwalarsu”
“Subhanallazi lam yattakiz waladan walam yakun lahu sharikun fil mulki walam yakun lahu waliyyun minazzull” ta furta wasu hawaye masu sanyi suna sauko mata. Tayi tunanin zasu tsaya amma basu tsaya din ba,haka suka dinga sauko mata daya bayan daya. Bai hanata ba Dr,yadai miqa mata tissue yana duba wasu ayyuka nashi har sai da zuciyarta tayi sanyi sannan suka dakata,ta gyara fuskarta ta kuma gyara zaman mayafinta sannan tace
“Amma Dr ina tsoro,ta yaya sultana zata iya haifan tagwaye da kanta?” File din gabansa ya rufe yana dubanta
“Bayanin da nakeson miki kenan,tayi qanqanta qwarai,don ko a yanzun girman da yaran keyi a cikinta ya bani mamaki,nauyinsu da na gani,lallai ita kanta ba qaramin qoqari takeyi ba,kuma tana da jarumta duk raunin nan nata da yawan koke koke,bakinta kuma na tabbatar duk da yawan qorafinta akwai abinda bata iya gaya miki,so ina kyautata zaton cikin yana shiga sati na talatin da shida za’a yi mata CS a cireshi……amma banason ki gaya mata hakan,saboda a yanzun dole a dinga monitoring blood pressure nata,a bata kwanciyar hankali sosai da nutsuwa don komai yazo yadda akeso”. Sosai jikin ama ya qara sanyi,ya lura da hakan sai ya bata gwarin gwiwa sosai,qwarin gwiwar da ta sanya taji eh tabbas zasu iya fuskantar komai,kuma komai zaizo ya wuce da qudirar Allah kaman bai faru ba.
A karo na Babu adadi bayan fitowarta daga office din Dr abdur'razaq ta ciro wayarta,kamar kowanne lokaci da idan abu irin hakan ta faru zatayi gajeran tex wa maina
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 23
A duk sanda wani abu ya faru sai ta rubuta ta tura masa tare da gargadinsa kan duk inda yake ya dawo. Ko sau daya bata taba samun tabbacin saqon yana isa ba,bata taba ganin alamu na maido amsa ba koda da digo,amma hakan bai hanata aika saqon ba.
Cikin hanya kaf tunaninta na yadda zata sake dauke hankalin sultana,tare da yin handling komai idan lokaci yayi.
Dukka qarfi da basirarta ta sanya don tabbatar da farincikin sultanan. Ta sake qirqirar abubuwan da tasan zasu dauke mata hankali. Tilas ta dinga siyan ticket na zuwa qasashen da suke maqwaftaka da Austria duk don ta faranta ranta,ta kuma sake don a samu a cimma nasara.
****Misalin qarfe tara na dare ta fito daga toilet din. Daure da babban towel take amma sam ya kasa ratsata saboda girman uban cikin dake gabanta. Da qyar take daga qafafunta,duk ta qarasa zama wata babba ta kuma kumbure har fuskarta. Dazu daxu kafin ta shiga wankan ta gama cikin kukanta,abinda ya ruruta idanunta kenan,ya kuma sanya fuskarta ta sake yin jazur.
Kai tsaye ta isa gaban mudubin ta tsaya tana kallon kanta da kanta,wani zazzafan hawayen ya zake silmiyo mata,ganin kanta takeyi kamar ba ita ba,sau tari idan ta kalli fuskarta takanji kamar ba itace sultana ba,itakam a rayuwa tana jin hatta da shaidan saidai maina ya biyo bayan qiyayyarsa a zuciyarta. Batajin har abada zata iya yafe masa,batajin akwai wani wahala ko Azaba da zata ganshi a ciki da zai karya zuciyarta taji zata yafe masa. Kullum kwanan duniya fadi take fili da zuci
“Allah ka sakamin”. Hannu ta saka ta yaye towel din,tulelen cikinta dake rinjayarta ya bayyana,yayi girma qwarai ya kuma yi tsini sosai,ta dafe qasan mararta da nauyin da takeji yafi yawa a nan akan ko ina,Allah Allah takeyi kwanan watan da ama tace mata zata karbi babyn yayi,Allah Allah take a cire mata shi,ta hanci ne?,ta baki ne?,ta kunne ne oho itadai ba matsalarta bane. Matsalarta daya ta wayi gari ta jita wayau,ta jita ta tashi babu wadannan lalure laluren da uban nauyin da yake damunta.
Turo qofar da akayi ya sanyata saurin sakin towel din. Ama ce ta kuma ga abinda ta tsaya din tana kalla amma sai tayi kamar bata gani ba,ta dauke kanta ta shigo dakin tana fadin
“Bakijin sanyi sanyin garin nan daya fara busawa?”
“Yanzu zan shirya” ta fadi da dakusashiyar muryar da har yau bata bude qwarai ba don ba maganar ma ta fiya yi ba bare ta bude yadda ya kamata.
Tana kallon ama ta gefen ido ta jawo akwatin da kusan kullum sai taga tazo ta shiryashi,ta kuma sake zuba kaya,ita kadai cikin ranta take mamakin kayan da ama din keta narkawa akwatin,bayan tace mata dashi zasu tafi asibitin,to tabbata zasuyi cikin asibitin da aketa loda ma akwati kaya?,oho bata da wannan amsar,sai kawai ta jawo lotion ta fara shafawa a jikinta.
*Sanye da kayan theatre Dr abdur’razaq mansoor ke fitowa daga office dinsa. Gefansa wani gajeran likita ne baturen qasar Austria din,yana riqe da files a hannunsa suna magana da Dr abdur’razaq din cikin harshen German.
Ama dake zaune saman kujerun dake daura da theatre room din ta miqe tsaye tana jiran qarasowarsa. Dab da zasu iso din ya sallami likitan ya shige dakin theatre din shi kuma ya amshi file din hannunsa yana qarasowa.
Yaga fargaba,sarewa da kuma tsoro a tattare da ita,abinda bai tana gani ba kenan daga gareta tsahon watannin da sukayi suna zuwa gurin nasa. Tsayyayyar macace da ba komai ke firgitata ko kuma ya bata tsoro ba. Ya sani a irin situation din sultana dole ta fuskanci fargaba da tsoro,don haka ya sakar mata murmushin dake bada qwarin gwiwa,ya miqa mata file din yana kallon agogon hannunsa
“Ki kiranta a nutse ki sanya hannu,sanya hannun shi zai bamu damar fiddo miki jikokinki nan da mintuna talatin kacal in sha Allah”. Hannu tasa ta amsa,ta koma ta zauna kusa da tanja gwiwa a matuqar sanyaye,ta buda page din ta fara karantawar tana sanya hannu,saidai a duk inda ta sanya hannun,sai zuciyarta ta jaddada mata…..muddin aka samu akasi la shakka itace ta kashe sultana
“Hasbunallahu wani’imal wakil” take bin mummunan tunanin da shi,har ta kammala ta rufe ta miqawa Dr abdur’razaq. Amsa yayi yana sake murmushi
“Compte à rebours les minutes(ki irga mintunan)” ya fadi yana bata qwarin gwiwa cikin idanunsa,sannan ya taka zuwa qofar dakin theater din ya sanya kai bakinsa dauke da bismillah.
Ragwaf ta koma ta zauna,ta dunqule dukka hannayenta cikin na juna tana jin jikinta yana mata wani yaarr,ta dinga maimaita kiran sunan Allah data samu bakinta ya fuzgo sanda tanja dake riqe da carbi take maimaitawa a fili don ta samu ama din ta kama kuma nutsuwarta ta dawo.
Mintina biyar kacal ambaton sunan Allah ya saukar mata da nutsuwa,saita zaro wayarta as usual ta turawa maina tex akan current situation din da ake ciki,ta maida wayar tsakanin cinyoyinta kawai tana ci gaba da kiran Allah.
Da ita da bibi batasan waye ya riga wani miqewa ba sanda qofar theater din ya bude ba,saboda mintunan da Dr abdur'razaq mansoor ya basu sun cika harma sun gota da wajen qarin mintuna wasu talatin din akai.
Dr dinne da kansa,iya fara'ar saman fuskarsa kawai ta bayyana musu labarin me dadi ne,ya qaraso gabansu yana cire facemask din fuskarshi
“Alhamdulillah,anyi nasara,an ciro mata tagwaye dukka YARA MATA” ya fadi yana duban tanja da ta qame cikin zallar farinciki.
Batasan yaushe bane,ba kuma tasan ya akayi ba,itadai taji dukka gwiwoyinta sun zube izuwa qasa,kafin daga bisani fuskarta da goshinta su kafu a qasa
“ALLAH kaine Allah,Allah ina me tuba izuwa gareka,Allah na tuba bisa dukka laifukana,Allah na tuba bisa dukka zunubaina,Allah na tuba bisa karan tsaye da nake yiwa al’amuranka, ubangiji a yau ka tabbatar min da qarfin ikonka,Allah ina godiya a gareka,Allah na gode mahaliccina na gode,ya hayyu ya qayyumu kasa yarannan rayayyu ne,duk wani dake boye da wanda ke a zahiri Allah ya daidaitashi cikin izza hikima da buwayarka,Allah ka bawa mahaifiyarsu dangana,ka bata haquri,ka taushi zuciyarta,ya hayyu ya qayyumu ka karkato da hankalin mahaifinsu gida,Allah kaine mafi sani,kafi kowa sanin hikimar data sanya ka wanzar da wannan al’amari,ya arhamar rahimeen ka sanya qarshen komai ya zamana da kyakkyawar cikawa” sannan ta cikashe da maimaita alhamdulillah har sau babu adadi.
Itama tanjan sumbatun addu'a kawai ta dinga yi,hawaye ne itama cikin idanunta,yau 'yar lelen bibi ta zama uwa,yau 'yar lelen bibi da yara har biyu?,tabbas wannan haihuwa inda cikin gida nijer akayita batasan wanne irin cika yau asibitin nan zaiyi ba,batasan adadin farincikin da fuskokin mutane zasu nuna ba.
Da suka buqaci ganinta ba'a hanasu ba,wata nurse ta musu jagora zuwa dakin hutun da aka bata wanda suna ciki ita da yaran da aka dawo dasu daga sashen yara yanzu yanzu bayan anyi musu gwaje gwaje da bin qwaqwafi irin na bature. Sakamakon da suka gani ya basu mamaki kodon qarancin shekarun uwar yaran. Sun jima basuga lafiyayyun yara irin yaran ba,ga wani irin girma kai baka ce daga cikin qaramar yarinya under 14yrs suka fito ba.(ai addu'a ba wasa bace,duk wanda ya gaza ganin tasirin addu'ar da yakeyi to baiyi addu'ar da kyau bane,ko bai cika sharuddanta ba,ko kuma baiyi addu'ar yana bawa Allah dukkan yaqininsa ba da yardarsa ba).
Duk yadda taso taje ta fara ganin fuskar sultana dake bacci daga ita har tanja sun kasa,gaba dayansu gadon babies din suka nufa,hannun kowa yana rawa yana saurin isa garesu.
“Ma sha Allahu la quwwata illa billa,ma sha Allah….tabarakallahu ahsanul khaliqeen…..” Ama ta dinga maimaitawa bakinta yana rawa.
Wasu irin fararen yara masu cikar zati da kyau,wasu irin jarirai masu tsananin kama da juna,kyawawan jariran da batasan ma kamannin waye zatace sun dauko ba. Farare tasssss tamkar iyayensu haifaffun Vienna ne ba nijer ba,nannade cikin fararen kaya masu tsananin taushi da daukan idanu.
Yadda hannunta ke rawa ta tabbatar muddin ta daukesu tana iya yada su,hasalima bata iya gani sosai saboda uban hawayen dake narke cikin idanunta,saita sanya dogayen yatsunta ta riqe siraran yatsun yaran dake nannade cikin safar hannu. Duk yadda taso riqe kanta sai ta kasa,kuka ya balle mata,tayi qas da kanta tana kokawa,tanja tana bata baki.
Ina maina ya tafi?,ina aliyyu yaje?,yazo ya gani a yau shima ya zama uba,a yau yabar yabanya,a yau ubangiji ya cika masa burinsa,mafarkinsa,kuma fatansa,burin da a sansa yake furtawar yana fada ne kawai ba tare da samun tabbacin fatansa zai cika ba
“duk randa nayi aure,matata ta haifami ‘ya mace haihuwar fari ama ke zan bawa,in sha Allah sai na share miki kukan rashin haihuwar ‘ya’ya mata,sai na dauke miki takaicin da ake sakaki na hanaki riqon ‘ya’yan wasu” wasu daga cikin kalaman maina kenan a duk sanda yaga tana neman ‘yar budurwar da zata riqe,ko kuma taje ta daukota akazo aka karbeta,ko kuma ta fara riqon taje hutu taqi dawowa. Yau gashi burin maina ya cika,bama yarinya daya ba,yara biyu reras a lokaci guda,itakam batasan me zata cewa Allah ba.
Ko sau daya ama ta kasa motsawa daga gindin gadon,ta kasa dauke idanunta daga kan yaran,duk wani motsi da zasuyi saman idanunta ne,kamannin yaran sun baci ainun. Wata irin mahaukaciyar soyayyarsu ce ke ratsata tun sanda ta dora idanunta saman fuskarsu,sai takejin kamar a duniya bata taba son wata halitta ba tunda Allah ya halicceta sai a kansu.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 page 24
A hankali ta zare hannunta daga nasu bayan sunsha hoto,sun sha videos har batasan adadinsu ba,ta matsa kusa da sultana karo na biyu taga kota farka a baccin?. Har yanxu dai baccin takeyi lakadan,fuskarnan ta fada tayi kuyas,hakanan duk girman jikinnan ksmaryan zugeshi tare yaran,ta ragu sosai,qanqantarta ta soma dawowa.
Sai data fuskanci lokacin sallar azahar yayi sannan ta tashi a wajen,ta shiga bandaki ta daura alwala tabar tanja a wajen.
Sanda take idar da sallar sultana ta motsa,ta shafa addu'ar da sauri ta miqe ta nufi sultanan.
Tun daga idanunta zuwa jikinta take jinsu wani iri,batayi yunqurin miqewa ba saboda nauyin da jikinta yayi mata,kanta ta mirgina gefe guda tana kiran Allah can qasan zuciyarta,zuciyar tana bata zaiyi wuya idan ba mutuwa tayi ba,don ba abinda zata iya tunawa,tadai jita daga qarshe kamar tana yawo cikin iska.
Ama data hango tana tahowa ta tsurawa idanu. Da murmushi a fuskarta ta taqaraso,ta jawo doguwar stool dab da gadon nata ta zauna. Idanunsu cikin na juna
Hannunta ta miqa ta riqe hannun sultana wanda babu qarin ruwa a jiki
“Kin tashi?” Kai gyada mata tana ci gaba da duban ama din
“Sannu” yauwa tace da ama,amma sautin baya fita sosai.
“Me yake miki ciwo yanzu?” Kai ta girgiza alamun ba komai,hakan ya yiwa ama dadi,sai taci gaba da zama a nan din bata sake cewa komai ba kaman yadda sultana din itama bata sake magana ba,sai idanunta data mayar ta lumshe. Tana jin alamun cikinta empty babu komai,duk uban nauyin dake jibge tana jin ba komai a cikinsa,tasan dai kenan tabbas an cire baby din kamar yadda ama tace mata,to amma yana ina?, Ta yiwa kanta tambayar
“Oho” ta sake baiwa kanta amsa
“Kome meye na cika umarnin ama,nima ama ta cikamin alqawarina,ban mutu ba gani ina raye,baby dama nasu ne,na gama nawa aikin” ta gayawa kanta da kanta,don haka tayi relax daga kwancen,duk da tanajin ta soma gajiya da kwanciyar.
Qushin qushin din qananun kukan jariri shi ya sanyata bude idanunta a hankali,saidai kuma bata yarda ta juyar da kanta sashen da take jiyo kukan ba
“Hajja yaran nan fa da alama maciya ne,tun dazu sun kasa nutsuwa sai mutsu mutsu sukeyi,ya kamata a nema wani abun a basu,tunda naji kince likita yace idan sun nema din a basu” tanja dake rungume da daya daga cikinsu ta fada
“Eh,ai bari nazo nayi musu addu’a cikin kunnensu” ta fada tana zame hannunta daga na sultana.
“Har su nawa ne?” Sultana ta yiwa kanta tambayar can qasan zuciyarta,duk takun ama zuwa wajen yana qididdige a kunnenta
“Wacece babba ne?” Tanja ta tambayi ama tana duban fuskokin yaran
“Akwai alama da suka sanya a qafafunsu”aman ta fada tana duban qafafun yaran.
“Ga hassana ga usaina” ama ta furta tana murmushi hadi da duban fuskansu.
“Anya wannan nan gaba za’a dinga banbancesu?” Fuskokinsu ama ta duba sosai
“Subhanallah subhanallah” aman ta fadi da sauri tare da yiwa tanja nuni da hannu. Daidai gefen kunnen hassana,wani digon baqi sak irin na maina
“Tanja kin gane wannan?” Ama ta fadi muryarta tana dan rawa,abinda ya sanya sultana bude idanunta da sauri,ta kuma juyar da kanta sassan da su ama ke tsaye tana ware idanunta cikin fargaba
“Allah hakimu,Allah me iko,irin digon baqin dake kunnen maina” da sauri sultana ta runtse idanunta saboda kiran sunan maina din, tsakiyar qahon zuciyarta taji kamar an caketa da wani qarfe. Tanason saka hannuwanta ta toshe kunnenta don kada ta sakeyin kuskuren jin sunansa ko wani abu da yayi kamanceceniya da shi,saidai a daidai lokacin ama ta yiwa tanja alama da idanu na kuskuren kiran sunan nasa da tayi,don haka tanja din bata sake cewa komai ba,sai ama data miqa hannu ta karbi yaran ta sanyasu cikin jikinta sosai,dumin jikinsu yana haduwa,wani irin qauna ta jini tana ratsata.
Dukka addu'o'in da musulunci ya tanada tayi musu,ta kuma yi musu huduba cikin kunnuwansu,sannan ta basu suna kanta tsaye ba tare da shawara da kowa ba FATIMA BINTOU DA NADEEYA (mahaifiyar sultana da kakarsu aba). Hadasu tayi dukka ta sake rungumesu a jikinta tana sauke ajiyar zuciya. Ko yau ta mutu burinta ya cika,babu kuma abinda zata cewa ubangiji face godiya mara qarewa.
“FATIMA BATOUL da NADEEYA BENAZEER” Ama ta fadi idanunta akan fuskarsu. Masu cikakken gata irin gata da ba kowanne bawa Allah ke tsagawa da rabonshi ba,amma sai gashi sunxo tsakiyar wata irin cudewa rikita rikita da kuma cakwakiya,saidai koma meye ita din ba zata bari komai ya shafi rayuwarsu ba,zata basu cikakken gatan da suka cancanci dashi,zata basu dukkan wata rayuwa da duk wani me tutiya da tunqahon gata zai sameta.
Har likita ya bada umarnin sultana zata iya zama zata kuma iya miqewa,sannan ya bada umarnin duka a ranar za'a iya goge mata jikinta,za'a kuma iya nema mata wani abu me ruwa ruwa tasha bata tambayi yaran ba ko sau daya. Duk ama na ankara da ita,ko sashen da suke bata kalla,sai tayi mata shuru batace da ita komai ba,har sai data gama goge mata jikin,ta zaunar da ita tana bata abu me dumi. Dab da sultana din take zaune,ta miqa mata spoon bakinta sannan tace
“Baki tambaya baby ba sultana uhmmmm” shuru ta danyi,sannan ta bude bakinta a hankali
“Naki ne ama,dama kince ke zan bawa,na bakin ai” kai ama din ta jinjina tana jin ba dadi,kada dai ya zamana su rasa soyayyarta kamar yadda taketa tunani tun dazu.
Rabuwa tayi da ita har sai data gama batan sannan ta maida bowl din. Ta qarasa inda yaran suke ta dauki batoul sannan tanja ta aza mata benazeer ta rungumosu a kafadanta.
Da idanu sultana ta bita sanda take aza mata yaran saman cinyoyinta,bata budesu ba ta kalleta tana murmushi
“Budesu ki gansu” cewar ama. Idanu biyu dukka sultana ta fiddo,sai kuma ga hawayen nan nata da bata gajiya da xubdashi
“Har biyu ama?,ni ba guda daya kikacemin bane?,har guda biyu?, gaskiya ni guda daya ne…..guda daya ne Allah” mamakin tarin quruciya irin ta sultana da bata rabuwa da ita ya kama ama
“To biyu Allah ya baki,yanzu a ciki wanne ne bake kika haifa ba?,wace bakyaso?,bude ki kalla ki zaba na zaba a bada dayan,dayar kuma saiki bata nono kinji kinga duk yunwa sukeji” kuka ne ya qwace mata
“Ni banaso duka,banaso ama,kuma ba Wanda zan bawa…….” Sai ta kasa qarasa fadin nonon ta sanya hannunta mara qarin ruwan tana janye zaninta,abinda ya sanya batoul ta gangaro sosai jikin benazeer,nauyinta kuma ya sanya benazeer ta gaza riqeta suka fara gangarowa.
A gigice ama ta sanya hannayenta ta fada tallafe yaran zuciyarta na bugawa da tsananin tsoro,saboda ba qaramin shammatarta tayi ba,dukkansu yaran suka tsanyare da kuka a lokaci guda,da alama suma din sun tsorata dinne.
Wani irin mummunan baci ran ama yayi,bata tabajin haushin sultana ba irin yau,bata taba jin rayukanta sun baci dama ko meye takeyi ba irin yau.
“Ke sultana!” Ta kirayeta cikin tsawa,tsawar data kada zuciyar sultana din. Karo na farko a rayuwarta da tsawa ya taba hadasu da ama
“Ashe baki da hankali?,don baki sonsu sai akace ki kashesu?,yaran da kika haifa a cikin cikinki?,ke haka kika ga bibi tana miki?,haka kika ga aba yana miki?, oncle bashar oncle umar?,uwa uba mahaifin nasu da kikaqi jini?,shi ya goyeki a gadon bayanshi,ya baki abinci da hannunsa,yayi maka wanka,wankin kashi da na fitsari,shine yanzun zaki gangaro qananun yara da ko kwana daya basuyi ba duniya?,to ke kika haifesu duka ‘ya’yanki ne,idan ke kika haliccesu ki maidasu inda suka fito” ta qarasa fada cikin bacin rai tana debe yaran.
Wani mugun mutuwa jikin sultanan yayi,dukka gabbanta sukayi sanyi,idanunta suka cicciko da sabbin hawaye,ranta ya dinga yi mata ba dadi da ganin bacin ran ama. A yau zuciyarta ke mata fadan da ya dace,bai kyautu ta yiwa ama haka ba,matar data tsaya da ita cikin wuya rintsi da dukka tsananin data fuskanta tsahon watanni goma,bata tana gajiya ba,bata taba sarewa ba,bata kuma taba ja da baya ba,bai kamata ta saka mata da wannan ba.
Tana jin sanda ama ta fita ta siyo madara tazo ta hada ta bawa yaran,babu jimawa sukayi luf,bacci yayi awon gaba dasu.
Ama bata sake saurarenta ba,iyakaci ta barta da tanja,tana ji tana gayawa tanja ita yanzun ta koma rainon jikokinta,ga diyarsu nan. Abun sai ya quntatawa sultana,a fakaice dai ama ta rabu da ita kenan?. Ko a washegari da mutane sukayita shigowa ganin twins duk wanda ya tambayi mamansu sai tace bacci takeyi,duk kuwa da idanunta biyu. Sosai turawan suka dinga shigowa ganin 'yan biyu,abinka da bature wanda baya raina abun kallo. Hotuna suka dinga yi da yaran,gif kuwa sai gashi sun cika wani sashe na dakin da gifts,har sai da ma'aikata suka kwashe aka kai musu ajiya dakin ajiya dake cikin asibitin. Wani irin kyau da murjewa yaran sukeyi,kusan kullum Allah ne da kullum amma indai rana zata fito ta fadi sai masu son ganin yaran sun shigo,kuma dukkansu turawa ne,duk wanda zai shigo kuma da gift dinsa,suna son yaran kamar su lashesu,akwai cikin ma'aikatansu da kullum a rana sai sun shigo kusan sau uku kawai saboda yaran,tamkar wadanda aka yiwa yayyafin farinjini,ita dai ama ta sani muddin suka dauko farinjinin iyayensu to lallai sai ta hada musu da addu'ar baki.
Kwana uku kacal suka sallamesu,har a ranar aman bata sake mata maganarsu ko tayin basu nono ba,hasalima ita da yaran saidai taji muryoyinsu daga nesa,suna qushin qushin din kuka ko wani abu daban.
Bata yarda ankai yaran ko ina na,cikin nan dakinsa tasa aka shirya musu gadajensu da komai da komai,komai nasu pink hot pink da baby pink,komai nasu designers ne,hatta da turaren jarirai na kamfanin Dior ta siya masu yawa ta ajjiye. Dukka kayan sawarsu kuwa cotton kaya ne masu kyau qwarai 'yan turkey,channel brand,h&m brand,zara brand,Lacoste fendi Balenciaga da sauran manyan brand. Tanason a san cewa tabbas daga tsatso da ahalin manyan iyali suka fito MAYAK'I FAMILY sannan jinin babbar 'yar kasuwar qasar nijer da kewayenta hamdiyya ABDU ME KANO ne.
Tsaf ta shiryasu cikin wasu long sleeve body suit masu kyau da taushi na kamfanin channel,ta nade kowannensu cikin shawl me taushi sannan ta rungumosu kowacce ta kwantar da ita saman gadonta,ta daidaita qarfin AC din dakin,sannan ta fita zuwa kitchen don ta zuba ruwan zafi a flask dinsu ta hada musu madara.
NADEEYA ALIYYU MAYAK’I (BENAZEER)
FATIMA ALIYYU MAYAK’I (BATOUL)
SAI MUCE BARKANKU DA ISOWA TSAKANIN CAKWAKIYAR DADDY MAINA DA MOMMY SULTANA😂😂😄
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 25
Ta dade a tsaye gaban madubi daure da towel,ita bata shirya ba ita bata zauna ba,haka kawai takejin zuciyarta wani irin empty,sai tarin karaya da rashin confidence. Sake shafa fuskarta tayi a karo na babu adadi tanason tuna fuskokin yaran,batasan me takeji a kansu ba,soyayya ko qiyayya?,har yanzu bata tantance ba,abu daya ta sani har yanzu tana iya tuna wahalar da tasha a kansu,ko yanzu da take goge jikinta sai data kalli wajen da aka yanka cikin cikinta saboda yaran
“Mene makomata?” Tambayar da taketa yawaita yiwa kanta kenan,zata koma nijer ne taci gaba da fuskantar mutane?,taci gaba da fuskantar qawayenta a haka?,da wacce fuskar?,ita sultana me ‘ya’ya har guda biyu?,duk da ama ta karbesu,duk da ama tace nata ne amma ta sani hakan bazai canzasu daga sunan ‘ya’yanta ba tabbas!. Wanne bigire ta kama?,ina rayuwarta ta fuskanta?,bata sani ba!,bata sani ba sam sam sam……wannan itace amsar da take bawa kanta.
Qas tayi da kanta, hawayen da batasan ranar daina zubarsu ba suka fara tsiyaya daga idanunta suna diga saman madubin.
Sautin kukansu cikin muryar rigima sosai ita ta sanyata daga kan nata tana duban fuskarta ta cikin mudubin tamkar su din zata gani ta ciki. Idanunta ta maida ta lumshe kukan nasu na isketa har inda take,dukansu su biyun sun dage sai qyaqyata kuka sukeyi. Idanunta ta lumshe,batasan me yasa sam batason jin kukan ba,ta matsa daga gaban madubin,saita samu kanta da jawo babban mayafinta ta lullube dukkan jikinta,sannan ta taka a hankali ta murda qofarta ta fice.
Daga dakin ama ne kukan ke fita,ci gaba tayi da nufar dakin amma gabanta yana dukan tara tara,wata zuciyar kuma na hanata zuwan,sai ta kasa dakatawa,har ta isa qofar dakin ta tura ta bude.
Kanta ta fara zurawa tana leqensu,ba kowa cikin dakin sai su kadai,sun rude da kuka abinsu suna jejjefa qafa kamar zasu tashi sama
“Ya salam ya Allah” ta fada qasa qasa saboda yadda taji zuciyarta na motsuwa. Batayi tunanin komai ba ta sanya kanta cikin dakin,ta taka a hankali zuwa gaban gadajensu.
Fes kyawawan fuskokinsu suke,ba hawaye ko wani abu,harararsu tayi tana tura baki gaba,kamar an gaya musu wacece ita,kamar an sanar musu da matsayinta garesu sai kukan nasu yana baya sosai,da kadan da kadan yana ja baya,yayin da duk su biyun suka kafeta da idanunsu.
Itama nata idanun ta zube musu, zuciyarta na ayyana mata abubuwa iri daban daban. Banda wahalar da ita daya tasan kalarta da tasha, tabbas da zatace ba yaranta bane. Dan mutum guda guda har guda biyu?. Murmushi ya subuce a saman fuskarta karon farko bayan shudewar watanni d'ai d'ai har kusan wata goma sha daya rabon da ya fita a fuskarta. Miqa musu yatsuntsa tayi d'ai d'ai kowanne ta cusa shi tsakiyar tattausan tafukan hannunsu. Mamaki ya kamata yadda taji caraf kowacce ta riqe suka sakeyin relaxing suna kallonta zaka rantse ba jariran kwanaki kadan bane.
“Batoul?, benazeer?” Ta furta qasa qasa tana nuna kowacce da yatsa daidai,tanason ganin ta banbance sunayen kowaccensu?. Kai ta girgiza tana ganin kamar bata fadi dai dai ba,amma ta tuna taji ama tana cewa gefan kunnen babbar akwai alama irinta aliyyu. Wani daci ya ratsa harshenta da tuna sunansa kawai da tayi, qirjinta na quntata ta sanya hannu ta duba gefan fuskokinsu. Taga alamar da ama din ke fada,kuma haka yake,sak irin nashi,tawadar Allah,tasha tambayarsa meye wannan tare da nacin sai ta kankare masa
“Nadeeya BENAZEER fatima BATOUL” ta sake maimaitawa kamar me gudun kada ta mance sunan. Sai taji sunan kuwa ya zauna daram a kwanya da zuciyarta.
A nutse ama ta maida qofar ta rufe bayan ta gama kallon duk abinda takeyi. Sautin rufe qofar ya sanyata waiwayowa a dan razane gabanta yana faduwa. Ya akayi ta shigo haka ta sakankance ba tare da tunanin ama ko tanja wani cikinsu zai shigo ya ganta ba?. Kauda kai ama tayi sam kamar bata ganta cikin dakin ba,ta fiddo kyawawan feeders dinsu guda biyu ta dora saman bedside table tana nufar gadon nasu tare da fadin
“Bansan kun qagu kusha ba,ashe yunwa kukeji my babies” ta fadi tana fara dauko benazeer da kukanta yafi na kowa,sannan ta dauko batoul ta iso dasu gaban gadon.
Dole saidai ta fara bawa mutum daya,don tanja ke tayata bawa dayan tanjan kuma yanxu ta fita,don haka ta fara bawa benazeer sai kuma batoul ta fara qushin qushin. Da idanu sultana dake qame take satar kallonsu,shan madarar takeyi yarinyar sosai kamar zata hada da feeder din,da alama me cice sosai
“Wai mutum mutumin sultana aka shigomin da shi ne?,zonan ki zauna ki taimakawa batoul idan zaki iya” ama ta fadi tana gyara zamanta. A kunyace a kuma mugun darare ta tako ta zauna. Sau biyu tana miqa hannu zata dauki batoul sai ta fasa
“Har yanzu baki sonsu dinne?” Ama ta jefa mata tambayar da ta sanya babu shiri ta dauki BATOUL din ta aza saman cinyarta. Dumin jikin yarinyar ya sauka a dukka cinyoyinta,yarinyar kuma ta sake zuba mata idanu sosai kaman dazu,tamkar tasan yau ne ranar farko da mahaifiyarta ta azata zaman cinyarta,zata kuma shayar da ita da madara bawai da nonon jikinta ba.
Dukka yadda taga ama tanayi haka tayi,har sai da ama din tace ta zare ya isa haka,ta basu ruwan zam zam da shine ya ruwam shansu,kuma shi zaici gaba da zama ruwan shansu cewar ama har sai sanda suka buda baki sukace sun gaji dashi muddin tana raye.
“Sakata a kafada har sai tayi gyatsa” cikin tsoro ta dagatan ta sakatan,suka shiga shafa bayansu ita da ama din,sai a sannan ama ta magantu
“A qalla idan baki sosu ba ko kulawa ki nuna musu,mafi qaranci dai zasu tashi da ganin kallon rahama daga idanun uwarsu…….maraici bashi da dadi,ke baki sanshi bane saboda an baki cikakken kulawa da gata,to kiyi qoqari su dinma koda sun rasa uba susan cewa suna da uwa a raye”. Kasa cewa komai sultana tayi sai qas da tayi da kanta,wani abu yana dawainiya da zuciyarta.
Sanda ama ta lura batoul din tayi bacci tace ta kwantar da ita,lokacin da zata kwantar da itan kusa da 'yaruwarta ji tayi kamar kada ta kwantar da ita din
“zo ki zauna” ama ta sake fada kanta tsaye da daure fuska,daure fuskar da take sanya ma sultana shakkarta da kuma d’ari d’ari. A dararen ta zauna
“Ki saki jikinki sosai mana,ki manta ni momynki ce?” Maganar tayi mata dadi sosai,amma sai taji zuciyarta ta raunana,inda ace uwa mahaifiya a gareta tana raye wala’alla zatafi fahimtar duk wani rauni da quncinta ko?.
Kamar ama tasan abinda take tunani sai tace
“Zuwa yanzu banajin akwai wanda ya fahimceki kamar ni,akwai wanda zaisan ciwonki da zaqinki kamar ni……daga yau inaso sultana ta fara sauyawa,inason na daina ganin wannan sultanar,me musu da taurin kai,inason sassauqar sultana me cewa “eh to” a dukka lamuranta,inaso ki canza zan tallafa miki duk wani ciwo na zuciyarki ya gushe idan kin shirya” kai ta gyadawa ama tana share hawayenta
“Na shirya,kiyi haquri ama” ta fadi kuka yana tsinke mata. Cikin jikinta ta rungume sultana din tana rarrashinta. Sai takejin inama komai yazo ne a LOKACIN da ya dace,inama ace aliyyu baiyi gaggawa ba?,saidai idan ta tuns cewa rabonsu batoul……lokacin wanzuwarsu a duniya ne yayi shi yasa komai yazo a gaggauce irin haka,sai taji ta sake sallamawa lamarin ubangiji.
Hamdiyya abdu kano,jajirtacciya uwa kuma tsayayya. Itace ta shimfida dukkanin tafukan hannayenta......ta sadaukar da dukkanin dukiyarta........ta bada lokacinta da rayuwarta ma rayuwar SULTANA BATOUL DA BENAZEER.....ta sadaukar musu da dukka komai nata,ta kula da yaran ta kuma kula da uwarsu.
Dukkaninsu babu wanda ya samu naqasun kulawarta. Sau tari tanja kan zauna tayi shuruuu..... Eh lallai baka taba gama sanin halin mutum sai ka zauna dashi. Ashe wannan itace hamdiyya wato ama da sukewa kallon me izza,miskila saboda ganin ta mallaki maqudan kudade,wadda bata shiga shirgi ko sharafin kowa,ashe ita din me sadaukarwa ce,ashe ita din me sassauqar zuciya ce?.
Kulawa da sultana kusan itace ta kwashe mafi yawancin lokutanta. Fitness center ta kaita me kyau da suke bawa jikin sultana kulawa cikin kula da CS dinta ba tare da ya samu matsala ba,tanason sultanan ta koma sultana dinta,harma tafi da,tunda zuwa yanzun idan ka ganta zaka tsammaci ta shiga shekara ta sha bakwai ne bawai sha hudu ba. A gida kuwa lafiyayyun abinci da dukka nau'in ganye da tasan zai maida sultana mutum,ya murje mata jiki kullum cikin research da hade hadensu take,ruwan ganyen gwanda daya zamewa ama aboki a baya yanzun ta tilastawa sultana shanshi sau biyu a rana(yana hada nuna tsufa,yana maintaining jiki,kiyi looking younger akan shekarunki)daya daga cikin sirrikanta da take taqama dasu.
Sannu a hankali saiga sultana ta fara dawowa SULTANAN BIBI DA ABA,fatarta ta fara ninka kyanta,duk wata rama tata tana yin nata waje,komai yana komawa kan saitinsa. Tun usul dama damammen ciki gareta,don haka ko yanzunma ba zace ta taba daukan ciki a cikinta ba, stretch marks ne yaso fito mata dan kadan a fatar cikinta ama tace bataga ta zama ba. Kudi ta zuba sosai ta siya mata mayuka masu kyau da dan Karen tsadar da ko a can dimma saika ciza sannan zaka siya,sai gashi sun bace bat,babu su babu alamunsu,tunda dama bana halitt bane na ciki ne.
Gyaran kai, manicure da pedicure akai akai,so take ta koma sultana cikakkiyar 'yar gayu,cikin kwana talatin da biyar cif da haihuwar sai gata ta canza,ba zakace itace me jego ba.
Wani irin girma yaran sukeyi tamkar ba madara suke sha ba,wani irin wayo kai zaka ce sun doshi watanni uku ma. Bul bul dasu kamar ana hurasu, weather din Austria tamkar don saboda su aka halicceta. Wayo na masifa a cikinsu,sunsan idanun ama sunsan na tanja,don na sultana bai fiya ganuwa a garesu ba. Bata kyararsu,amma ba kasafai take shiga shirginsu ba,idan suna kuka dai takan daukesu idan ama bata wajen,amma indai tana wajen saidai ita ta dauka ko tanja.
Cikin kwanakin talatin da biyar din taji dukka hankalinta ya fara komawa gida. Ta yita duba saqonninta na layinta da email ko zata ga saqon sakinta daga hamid(aba) duk da tasan abune me wuya amma bata gani ba,sai saqon roqon ta dawo ta email dinta har babu adadi daga aba,saddi atta harma da almu.
Visa kawai ta shiga nema musu,tana ganin zuwa yanzu lokaci yayi da zasu koma. A yanzun zata koma da dukka qarfinta ne,zata sanya auduga ta toshe kunnuwanta,ta sanya duk wani effort nata ta nema inda maina yake,tana da buqatar danta,ba don komai ba kodon yaran da ya dasa baisan da wanzuwarsu ba,ya kamata su tashi da dumin ubansu. Ba zata sanya kowa neman maina ba,ita daya zata fuskanci komai,ita daya zatayi fadi tashinta,yadda suka dauki zafi dashi saidai suga dawowarsa gida......amma kuma hakan ba yana nufin itama ba zata hukuntashi ba bisa laifinsa,amma hukunci ta hanyar da ya dace.
Sultana batace komai ba bayan ama ta miqa mata passport dinta dake dauke da visa din Nigeria. Ta danji sassaucin ganin qasar nigeria zasu fara shiga,kwata kwata nijer ta fita a kanta, batasan ma ta yaya zata fuskanci rayuwa ba a can. Zaman gida zatayi tayi rainon yara?,ko makaranta zata koma cikin qawayenta da a yanzu ita kanta tasan tabbas ta banbanta dasu?,dukka dai bata sani ba.
****Sun baro Austria cikin matuqar kewa, Vienna garin da suka shuka tarihi a ciki suka kuma binne,sun fito da benazeer da batoul da a yanzun suke da shaidar zama cikakkun ‘yan qasar Austria halak malak,wanda sanadin haihuwarsu qasar ya basu wannan damar.
Transit ne na kwana guda a Egypt cairo,sun sauke luggage dinsu a gajiye,amma ama tace su shirya su fita su zagaya,akwai guraren tarihi me kyau da yake da kyau suje din. Tanja na murna ta gama shirinta,ta kamawa ama shirya su benazeer daketa wutsil wutsil abinsu,kamar sunsan suna kan hanyar komawa qasarsu ne.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 26
Sanda ama ta fito sultana na zaune ta saka tv a gaba tana kallon news,wanda ama tayi imani ba wani fahimtar me akeyi takeyi ba,kawai tsabar zama miskilar qarfi da yaji da tayi ne duk ta koma haka,bata doguwar magana bare doguwar hira,dukka kalmominta taqaitatattu ne
“Baki shirya ba sultana,ya kamata muje mu dawo da wuri mu kwanta don mu samu gobe mu tashi da wuri,jirgi baya jira” ama ta fadi tana taje doguwar sumarta
“Ama na gaji,saikun dawo” waiwayawa tayi ta dubeta
“Ahaaa?……kina da tabbacin sake samun dama irin haka?,baki da tabbas zaki sake ratsa qasarnan,oya tashi ki shirya” ta fadi tana dan dakewa. Tsam sultana din ta tashi,ama ta bita da kallo har ta shige bandaki.
Sanda ta fito cikin ido sai ama taga tayi mata kyau ainun. Cikin doguwar rigar Dubai,tayi rolling kaman yadda ta saba shekarun baya. Ta cika tayi tsaf tamkar babu wani abu dake damunta.
Yawo sukayi sosai gidajen tarihin dake cairo,sannu a hankali sai ta dinga jin zuciyarta na sakewa,damuwarta dake cunkushe a qirjinta tana raguwa sosai. Saidai duk inda duka gifta sai an tanka benazeer da batoul,abinda ya sanya dole ama ta sake lullubesu da kyau.
Koda suka shiga daya bangaren na kayan tarihi sai ama ta miqawa sultana batoul. Waiwayawa tayi ta dubi ama din,sai kuma ta sanya hannunta ta karbi yarinyar ta rungumeta a kafada. Ajiyar zuciya ta saki a boye,wani abu taji ya zarta ta jininta sanda dumin jikin yarinyar dake cakude da daddadan qamshin turaren Dior ya sauka a hancinta. Sau tari cikin zuciyarta takanji yaran suna burgeta,irin burgewa da kake iyaji ga yaran da suke ba naka ba ko kake ganinsu daga nesa. Tun daga ranar da suka iso duniya cikin ado suke da kwalliya,koda a gida suke babu inda zasu fita to tabbas adonsu na dabanne,hatta kayan bacci idan ka gansu a cikinsu saisun dauki hankalinka.
A asirce tanja ta saki murmushi tana kauda kai,wato dai so sone amma son kai yafi. Tuni ta lura da abinda ya sanya ama ta maqalawa sultana batoul,idanuwa ne sukayi yawa akan sultanar,duk da cewa ba wani sakewa a tattare da yanayinta ko fuskarta,amma ta fuskanci tana ta fusgar hankulan mazaje dake wajen.
Duk inda ama taga wulgawar kayan yara saita saiwa su benazeer,kayan qyale qyale masu yawa,su kadai take tunawa,komai ta siya nasu ne.
Sai cikin dare suka koma gida a gajiye,duk da haka ama bata gaji ba sai sata wanke yaran tsaf,nan suka shiga baccin gajiya.
****K’arfe daya na rana dai dai motar mallakin hajiya hamdiyya abdu me kano ke shiga makekiyar harabar gidanta dake garin abuja. Dukkansu ita da sultanan ba wanda bai saukar da boyayyar ajiyar zuciya ba.
Kafatanin masu aikinta maza da mata dukkansu suna tsaitsaye a harabar gidan domin yi mata barka da isowa. Sanda motar ta tsaya bakin motar sukayo,kowanne zuciyarsa fal farinciki da annashuwa,tsoro da fargabar data mamayesu na bacewarta tsahon watanni tuni suka bar zukatansu daga jiya data shaida musu isowarta,tare da isowar ma'aikata sukayi musayen furniture na gidan,suka kuma shirya lafiyayyen daki wa benazeer da batoul.
Bilki ce ta karbi batoul,uwa ta karbi benazeer kowa bakinsa fadi yake
“Masha Allahu,ma sha Allah,barka da arziqi sultana” a lokacin da sultanan ke fitowa daga motar cikin wata baqar doguwar riga me azabar sulbi da daukan idanu. Fatarta da jikinta dukka sunyi kyau,ta dan murje,saidai qiba ce har yanzu babu ita ba dalilinta,ta zama slimy.
A hankali idanun ama suka sauka kan baqin motoci da take gani a rumfar gidan,sai ta maida dubanta ga tasi'u
“Malam Tasiu wadannan motocin fa?” A ladabce ya rusuna yana cewa
“Yallabai ne suka zo shi da hajja bibi,yau kinsan ake bikin bude kamfaninsa na nan abuja” kai kawai ta gyada,ta san da company din,wanda ya dauki shekara da shekaru yana gininsa tare da tanadin ranar budesa,tabbatuwar kamfanin kuma zai iya sanyawa zamansu yafi yawa a Nigeria ne garin abuja saboda yawan hada hadar da a kullum aba din zai dinga gudanarwa.
Ciki dukkansu suka dunguma,tana jinsu bilki sun barke da hira da tanja hirar yaushe gamo?,sunata kwasar tanjar wai ta sauya quruciyarta ta dawo,itakam sai dariya kawai take musu.
Dukkan wani abu da zaiyi cikin watannin da sultana da ama sukayi baton dabo yana yinsu ne tuquru don wanke duk wani ciwo da radadi na batan sultana a zuciyar bibi. Ko a yanzun da duke dawowa su biyu rak cikin motar bayan ya karbi tuqin daga hannun driver dinsa ajiyar zuciya ta saki
“Har yanzu hamidou zuciyata ta kasa nutsuwa,har yanzu ina ganin cewa nice silar faruwar komai,inda nasan sultana na buqatar cikin,inda nasan da gaske hamdiyya take tana da buqatarsa itama,da na ajjiye nufi na,ba hamdiyya ba sultana….. shima maina tunda ya tafi…..”
“Ki ajjiye batun maina,ba mune mukayi masa laifi ba,shi yayi mana laifi,sannan ya zabi tafiya ya barmu,koda kasheta yayi a yanayin da ya barta bashi da asara” ya furta maganar yana ciro wayarsa da yaji alamun kira ya shigo. Baikai ga daga wayar ba kiran ya katse,sai text din hamdiyya da ya shigo kusan awanni biyu baya,rububin taro ya sanya bai gani ba sai yanzun da ya samu ya sullubewa jama’a yayi bad da bami a mota daya ya taho gida kawo bibi ta hut sannan ya koma.
Hannunsa har rawa yake sanda ya karanta layi guda kacal na saqon,ita dai bibi batasan me yake faruwa ba,taga dai ya qarawa motar uban gudu bayan ya aje wayar da hanzari a gefensa
“Lafiya hamidou?” Bibi ta tambayeshi tana dubansa
“Hamdiyya ce ta dawo,ina kyautata zaton suna nan cikin abuja” ya bata amsa yana sake bakwa kwalta hankalinsa sosai. Idanu bibi ta fidda cikin wani mugun zumudi da ba zata
“Hamdiyya?,ita da sultanan?”
“Eh na tabbatar tare suke” ya amsa mata yana sake qara tsula gudu abinda sam ba al’adarsa ba
“Allahu qadiran Ala man yasha’u” bibin ta furta hankalinta yana daguwa,jinta takeyi kamar tayi tsuntsuwa ta isa gidan,sai kawai tayi luf jikin kujera tana kiran sunayen Allah a jejjere.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA*
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 27
“a hankali bibi” aba ya fada lokacin da yake tsaida motar tasa bibi na qoqarin budewa ta sauka. Ai bata saurareshi ba sai data tabbatar qafafunta sun taka qasa. Da sauri ya fita a motar yabi bayanta,yasan tana da ciwon qafafu,a yadda kuma take gaggawar kaiwa ga sultana yana gudun kada ta sarqe.
Dukka muryarta ta ware tana doka sallama kamar baquwar gidan,ta daburce gaba daya,saboda batasan ta inda zata fara ganin sultana ba.
Tana shirin shiga wanka taji kamar muryar bibinta,kamar muryar da kullum take mafarkin ji,sai kawai ta jawo babban mayafi ta yafa a kanta tana nufar qofar fita.
Qarar bude qofar ya sanya bibi maida kallonta gurin,sultanarta ce,itama sultanan bibin take kallo,kallo kallon suka hau yiwa juna kamar wasu baqin juna,sai kuma daga bisani sultana din ta nufo bibi cikin sassarfa tana kiran sunanta da rawar murya.
Jikin bibi ta fada bibi din ta maida hannayenta ta rufeta gam
“Sultana?” Itama bibin ta dinga maimaitawa tana jin wani irin abu cikin zuciyarta,abinda ya karyar da zuciyartata kenan hawaye masu sanyi suka saukar mata.
“Bibi” itama ta sake maimaitawa kowannensu hawaye yana fita a idanunsa. Da kyau bibi ta riqeta suka qarasa saman kujera,sai kawai sultana din ta kifa kanta saman kafadarta tana sakin sabon kukan.
Ya zata iya kwatantawa bibi abubuwan data fuskanta?,baki bazai iya bayyanawa ba, gwagwarmayar data ratsa har ta kawo yau din ita kadai tasan abinda taji,ba mahalukin da zai iya fuskantarta,wannan din wani abune da yake tsakanin zuciya ruhi da kuma gangar jiki ne kawai.
Kasa cewa komai da ita bibi tayi,sai sharar hawayen itama da takeyi aba yana tsaye a kansu yana basu baki,saidai fiye da rabin hankalinsa shima yana tsakanin falon da kuma qofofin da falon ke dauke dashi,yana son ganin ta inda ama zata bullo.
Dukkaninsu taga shigowarsu ta cctv camera din dake hade da system din gefan gadonta,amma bata motsa ba,sai data kammala shirya yaran tsaf bayan ta musu wanka,ta nadesu cikin overall set da wasu irin huluna masu kyau da suka boye tattausan sumarsu me azabar baqi da sulbi,fuskokinsu sun fita tarwai da wani irin haiba da annuri.
Nannadesu tayi cikin tausasan shawl sannna ta sanyasu a kafadarta hagu da dama,ta zura slippers dinta ta taka zuwa hanyar fita.
Duk da cewa takunta baya bada wani sauti amma sai fitowarta din taja hankalin bibi da aba tamkar wadanda aka jonawa mayen qarfe. Kasa miqewa bibi tayi,daga ita har aba bin ama sukayi da kallo har zuwa sanda ta qaraso ainihin cikin falon da sallama a bakinta.
Wuce aba tayi kaman ma bata ganshi ba,ta isa gaban bibi a nutse ta sauke yaran daga kafadarta tana kwantar dasu a gaban ama tana jeresu daya kusa da dayar,sannan ta miqa hannunta tana yaye shawls din da suka lullube fuskokinsu.
Dukkaninsu suka kai idanunsu kan yaran,tamkar an jona musu shock haka sukaji cikin jikinsu
“Subhanallahi wabi hamdihi, subhanallahil azeem” bakin aba ya furta yana tasowa da gaggawa daga tsaiwar da yayi daga jikin bango.
Gaban yaran ya qaraso ya zube,yasa hannu ya tallafawa bibi da hannuwanta ke rawa tana son karbar yaran,ya dauki benazeer ya dora mata ita saman cinyarta.
“Ya Allahu,ya assamadu” shine abinda take maimaitawa tana juya yaran qwalla na sauko mata
“Astagfirullah, astagfirullah…..” Ta sake maimaitawa tana jin qirjinta na mata nauyi,har cikin jini da zuciyarta takejin wani irin nauyin ubangiji,har ruhinta takejin wata irin kunya tana saukar mata,yanzu wadannan halittun da taso a murqushe?, yanzu wadannan ruhin taso a niqeshi yabi rariya?.
“Allah na tuba,Allah ka yafemin,Allah kada ka barmu da soye soyen zukatanmu” ta dinga maimaitawa hawayenta yana qara yawa
Hannu ta miqa tana shafa fuskokin yaran,idanuwanta a kansu tana sake tsarkake girman zatin Allah.
“Ga jikokinku nan,kuma ‘ya’yan jikoki,wadanda kukaso gushewar rayuwarsu kafin isowarsu duniya,nayi dukkan abinda nakega ya dace nayi,ga sultana nan na dawo muku da ita,yaran kuma zan riqesu,Allah ya rayaminsu” ama ta fadi hawaye yana cika idanunta taf ta sanya tafin hannunta tana sharewa
“Inaaa hamdiyya,kece kika cancanci mu bawa haquri,kece kika cancanci wannan yabon,abinda ya kamata tunaninmu yakai kai ya gaza kaiwa kece naki tunanin yakai,kika fiddamu daga halaka zuwa hanyar tsira,inda ace na aikata abinda son zuciyata ya gayamin a sannan tabbas da zuwa yanzu ina cikin fushin Allah,ku yafemin ‘ya’yannan da naso kasheku tun baku shaqi iskar duniya ba” bibi ta fadi tana sake kuka.
Iya yadda bibi ta rame kadai ya isa ya gayama ama ba qaramin tashin hankali take ciki akan tafiyarsu ba. Cikin zuciyarta wani abu ya darsu me kama da tausayin bibi cikin ranta
“Zo nan hamdiyya,yaki” Bibi ta furta tana miqawa ama hannu. A nutse ta qarasa gaban bibin,ta tsugunna,har a yanzun tana jinta a matsayin suruka,kuma har yanzu babu abinda ya sauya. Ta sani dukkan wata zuciya cike take da son rai,saidai idan Allah ya baka ikon fin qarfin zuciyar taka.
“Allah yayi miki albarka,kiyi afuwa a gareni” bibi ta fadi tana dafa hannuwan ama. Qas tayi da kanta tana jin nauyin bibi din
“Ya wuce bibi,ya wuce har abada”
“Na gode hamdiyya” ta sake fadi tana sake duban fuskar yaran daya bayan daya,tare da tunanin da waye sukayi kama
“Wanne suna kika basu?” Bibi tayi tambayar sanda ama ke tashi ta zauna sosai saman kujera kamar yadda bibi ta buqata a tare da ita
“Nadeeya BENAZEER da Fatima BATOUL” a nutse aba ya daga kai ya dubeta karo na biyu yana jin kimarta na daduwa cikin ransa,yayi tsammanin zatayi zuciya ne,ta saka sunanta da kuma sunan duk wanda taga dama,sai gashi ta watsa komai a baya,ta sanya musu sunayen mutanen da suka kasance tsani na samuwarsu.
A hankali aba yakai bakinsa kunnen kowaccensu yayi mata addu'a,ya sauke batoul a nutse saman cinyar ama sanda ta fara mutsu mutsu yana miqewa idanunsa suna satar kallon ama. Ya sani akwai zantuka da yawa wadanda a yanzun ba zasu fadu ba,ba kuma zasu yiwu a tattauna ba,zai jira lokacin da ya dace.
Ta sani abinci suke da buqata a yanzun,don tunda suka taho daga Egypt bacci sukeyi abinsu basu buqaci madara ba,sai ama ta juya tana kallon tanja data rabe tana jin nauyi nauyin ama
“A sama musu ruwan zafi zan hada musu madara” dubanta bibi tayi
“Madara kaman yaya hamdiyya?,ko zasusha madara nono ai ya kamata a fara basu ko tukunna,idan basu qoshi ba saisu qara da madarar”
Ama bata dubi bibi ba tace
“Madarar sukesha,itace abincinsu” ta maidawa bibi amsa tana gyarawa benazeer kwanciya.
“Ina nonon uwarsu?” Maganar ta zowa sultana a bazata saboda ta tsammaci bibi zata bar maganar ne,sai gashi kuma ya jefo da wata tambayar.
Waiwayawa bibin tayi tana duban sultana,a hankali sultana din ta jawo gaban mayafin jikinta tana sake suturce qirjinta da bibi ke kalla
“Hamdiyya kada dai kicemin hanasu nono tayi” bibin ta fada da wani irin zafi a muryarta abun yana tabata. Kai ama ta girgiza
“A’ah,kawai dai bata taba gwadawa bane”
“To yau kuwa zata gwada yau dinnan” bibi ta furta da gaske tana zunkudawa gaba.
Dukka idanunta sultana ta fidda waje tana zarosu,nonon nata za'a zuqa kuma?,tashin hankali.
“Aje a nemo min wannan maganin duk inda yake a garin abuja,a fiddo da dukka bournvita din dake gidan nan da madara,daga yau zuwa safiya nakeso ruwan nono yazo yara su kama abinsu” sosai sultana ta sake gwalalo ido gabanta yana faduwa
“Da kin bari bibi,tunda sun riga sun saba da wannan ai….. Bakiga kuma yadda ya karbesu ba?” Ama fada tana tana fuskar bintou
“Kinga hamdiyya ki daina bata bakinki,darajar nonon uwa daban da madarar bature,kinsan Allah?, billahillazi daga yau su da madara saidai a matsayin ciko” kuka sultana ta saki tsoro yana kamata,yanzun ace nononta zasu tsotsa?, fisabilillahi har mutum biyu?,ta ina?.
“Don Allah bibi kiyi haquri”
“Yo ai bansan baki da imani ba,haba sultana,kece za’a ce kiyi haquri dai,don nono kaman sun shashi sun gama” idanu sultanan ta wuwwulga a falon,ba wani sauran me cetonta,aba ne ya rage dama,shi kuma tunda aka fara batun shayarwar ya fice.
Duk irin kukan da sultana keyi saboda tsananin tsoron shayarwar bai damu bibi ba,nan ta gwaggwafe hada wannan tsuma wancan,zuwa safiya sai ga nono yazo.
Bibi da kanta ta taka ta amso benazeer da batoul daga wajen ama,wadda tuni tayi musu wanka ta shiryasu tsaf sunata tashin qamshi sai tsotsar baki suke,da alama dama a yunwace suke. Qin bin bibi ama tayi kada tausayin sultana ya mata tasiri ta hana abinda ita kanta tasan shine dai dai,abinda ya sanya bata taba tilastata ta basu din ba alqawarin hakan ta yiwa kanta,kuma bata fatan hakan ya haifar mata da wani raunin cikin zuciya,ko taga kaman aman tana biyewa soye soyen zuciyarta ne tunda ita din bataso,biyayya kawai takeyi.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 28
Idanunta fal ruwan hawaye take kallon bibi sanda ta fara aza mata benazeer akan cinya
“Don Allah bibi,wallahi zafi zanji na sani,bazan iya basu ba”
“Zaki koya ne,kowa ma ai da haka yake koya” bibin ta fadi tana hade rai babu alamun wasa saman fuskarta
“Yalla, fito dashi ki basu ko nazo da kaina na basu,an baki shine don kiyi ado dashi a qirjinki dama?,fito dashi” bibin ta fada cikin fada da tsawa. Hannu ta saka tanason cirosu,amma rashin sabo ma ya sanya ta kasa yadda zata fiddosu din
“Bari dai kiga” bibi tace tana motsawa kusa da ita. Kuka ta saki sanda benazeer ta cafki maman ta fara tsotso kaman dama ta saba. Idanun yarinyar qur kan fuskar sultana kaman tasan ba da son ranta take bata maman ba. Tasha kuwa sosai,bibi ta dauketa ta saka batoul itama ta kama guda daya.
Kafin su gama hawaye shabe shabe akan fuskar sultana
“Yauwa to ma sha Allah” bibi ta furta tana daga yaran. Sai yanzu zuciyarta ta samu nutsuwa,ta sanya batoul a kafada tayi gyatsa sannan ta saka benazeer. A nan saman gadon sultana din ta kwantar dasu,tanayi tana qananun mitoci,abun ya qonawa sultana rai sosai,yanzun kenan ko damuwa da damuwarta bibi ta daina?,bibi da bata barinta tayi kuka yau itake kallonta tana kuka amma bata ko dubeta ba bare ta lallasheta?.
Bibi na fita ya tura qofar dakin ya shiga da sallama. Tana tsaye bakin mirror tana daura towel,tanason shiga tayi wanka tunda ta samu bibi ta dauki yaran kafin ta dawo mata dasu. Sau daya ta juyo ta kalleshi ta dauke kai tana ci gaba da abinda takeyi din. Ya taka ya matsa gabanta yana dubanta
“Hamdiyya” ya kirayeta qasa qasa
“Na’am” ta amsa masa ba tare data juyo ba,sai kuma shuru ya biyo baya
A nutse ya qaraso,ya jingina ta a jikinsa ta baya
“Har yanzu kina fushi ne?,kin daina ta tawa gaba daya sai ta jikokinki?” Bata dai waiwayo din ba ta bashi amsa
“Fushin me zanyi?, bayan nina muku laifi?,amma aina wanke kaina ko?,tunda ga diyarku nan na dawo muku da ita ban gutsireta ba”
“Ya isa” ya fada cikin son katse zancan,don gaba daya bayason ana maimaita maganar. Hannunta ya kama ya zaunar da ita sannan ya zauna a gabanta
“Haqiqa kinyi abu me kyau,kinyi abinda kika cancanci a yaba miki da kika tseratar da Bibi daga rudani da kuma fadama nadama,na gode miki qwarai,kuma ina fata zaki yafemin bisa duka kusakurai na” ta tsammaci zaya sako zancan maina amma sai taji bai sako din ba,ya zuwa sannan zuciyarta ta qeqashe da takejin bata buqatar taimakon kowa sai nata ita d’ai,don haka itama bata tada masa zancan komai ba.
Cikin kwanakin gaba daya tare da Bibi ake rainon yaran,sam sam ta hana a basu madara sai nono. Sultanan tayi kuka tayi kuka har idanunta ya dinga motsawa me ciwon amma hakan baisa bibi ta janye ba,duk sanda za'a basu nonon bibi ke tsaiwa a kanta saita tabbatar sun sha sun qoshi. Gaba daya jin abun take banbarakwai,abubuwan da take boyansu,abubuwan da take adonsu yau sun zama abebaden shan wadansu.
Amma kuma abun mamakin da yaran sun kama sun fara sha sai taji zafin da takeji cikin zuciyarta yana sauka a hankali. Wadansu irin yara ne,masu tarin wayo da wani irin farinjini da kwarjini da Allah ya zuba musu. Idan kana kallon fuskarsu ba zakaso ka daina ba,sun iya kallon mutum kamar sun sanshi ,bibi takance
“Wannan wayon da abinku aka haifeku,so kuke ma kufi uwarku wayo”.
Kwanansu uku kacal da dawowa saiga tawagar family din MAYAK'I sun iso. Kusan kaf kowa na gidan ba wanda aka bari acan. Duk wanda ya daga yaran sai yayi kamar bazai ajjiye ba. Sultana na daki kwance jikinta a mugun mace,ta kasa zama cikinsu,ta kuma kasa hada idanu da kowa,jinta take kamar bare a cikinsu,a dakin su aminata suka cimmata suna santin yaran
“Wallahi kaman ba kece mamarsu ba sultana,don Allah ki barmuna su kawai” kanta ta juyar wani sashen tana cewa
“Ku daukesu kawai na baku” dariya sosai yasmine ta saki
“Wallahi qarya kike,wai ke irin bakiso dinnan,wa zai samu yarannan yace baiso?,ko ke bakiso na tabbatar yaa maina yana son kayanshi” a wani irin fusace ta juyo da fuskar nata data kawar dazu tana kallon yasmine. Ambatar sunansa kawai dai dai yake da kira mata uwa uba da duk wani da take gani da kima a mazaunin mahaifi ka zageshi. Tashi tayi ta zauna sosai daga kwanciyar da tayi dazun tana duban yasmine
“Kada ki sake ki qara kiramin sunanshi a nan wajen yasmine,don ba wajen kiran sunansa bane nan din” tayi maganar kanta tsaye,idanunta na bayyana abinda ke danqare kai tsaye a zuciyarta. Sanyi jikin yasmine da aminata yayi,suka kalli juna,sai yasmine din ta koma ta zauna daga gefanta
“Kiyi haquri,mantawa nayi,amma sultana…..baki tunanin a tsahon wannan lokacin ma a ina yake?,kina da tabbacin kawo yanzu yana raye ko ya mutu?,kinsan yaa maina…..”
“Yasmine ya isa da Allah…..” Sultana ta fadi tana sanya yatsunta cikin kunnuwanta,da gaske take,batason jin komai da ya danganceshi,bata qaunar ambatar sunansa a gabanta.
Ama ce ta bude qofar dai dai maganar yasmine na qarshe data kirayi sunan maina. Taji komai ta kuma ga komai,sai ta saki qofar ta tako a hankali tana shigowa ciki
“Yasmine,kuje kuci abinci an kammala” miqewa sukayi dukansu,daya bayan daya suka fice a dakin,sai a sannan ama ta dawo da kallonta ga sultana.
Takawa tayi a hankali,ta sanya sannu ta zare hannuwan sultanar daga kunnenta. A nutse ta soma warware idanun nata ta saukesu a fuskar ama. Taga gaskiya muraran saman fuskar sultanar na iya girman tsanar data yiwa mainan,ta kuma tabbatar da gasken gaske take,don daga fuskarta har cikin idanunta sun canza launi zuwa ja.
Murmushi ama ta sake mata tana hadiye wani dunqulallen abu da ya tsaya mata a wuya. Habar sultanar ta dan riqe
“Karki sake damuwa,ba wanda zaya sake miki maganarsa,an rufe babinsa kinji?,tashi kiyi joining ‘yanuwanki kici abinci kema,ki sake a cikinsu,mutum kike kamar kowa,idan kina ganin abinda ya farun kamar ya rage daraja ko martabarki sam sam ba haka bane,a yanzunne ma kima da darajarki ta dagu,saboda kowa na miki kallon me hankali ne a yanzun,kina da abinda kaf ‘ya’yan jikoki babu me shi sai ke,tashi kije”. Da irin wadannan kalaman ama ta samu ta dinga rage mata kaifin abinda takeji cikin zuciyarta,ta dan sake dasu aminata tamkar suna gida tsahon kwanaki ukun da sukayi.
*Misalin bakwai da rabi na safiyar ranar lahadin,cikin gidan ama dake garin abuja,babban gid daya ginu ainun da wani irin tsari da kai tsaye idan ka kirashi da MANSION HOUSE bakayi kuskure ba.
Cikin faffadan dakin da ya zama masaukinsu najma aminata da yasmine,dukkansu a zaune suke kaman ba safiya ba,saboda shirin komawa nijer da sukeyi a yau din. Najma tayi wanka,aminata na zaune tana jiran yasmine ta fito ta shiga,sultana dake zaune saman sofa gab da aminata,sanye da wata rigar bacci me taushi me gajeran hannu da iyakar tsahonta gwiwa tana kallonsu kawai. Jifa jifa aminata na sanyata a hirartasu,gaba daya amsarta bata wuce daya zuwa biyu idan tayi nisa uku.
Sake kallonta aminata tayi,can qasan ranta tana mamakin sauyawar sultanar,a duniya duka idan akace mata wani lokaci zaizo da sultana zata zama miskila to tabbas zata musanta,musu kuma me tsanani,sai gashi dare daya sultanar ta tashi daga ainihin sultana ta zama wani abu daban. Sultana da a baya ko fada kakeyi da ita ta sanyaka kuka badai kai ka sakata kuka ba..... sultana da a baya idan ta fannin magana ne saidai ta cinyeka badai kai ka cinyeta ba.......saidai ka haqura kayi shuru ka barta......... saidai ka gaji kayi shuru badai ita ta gajiya ba.......yau sultana ce magana ke mata wuya,murmushi ya zama wani kayan gabas a wajenta
“Don Allah sultee……ki canza please,wannan sabon halin naki nikam baiyimin ba,kuma bayamin dadi” aminata ta fada tana bata fuska. Fararen idanunta kawai ta daga ta kalli aminata din sai ta maidasu ta lumshe. Aminatan ba zata taba ganewa ba,ba zata taba fahimtar what she goes through ba……a yanzun a cikin ruhinta itama jinta takeyi kaman ba sultana ba.
Kafin tace komai bibi ta shigo dakin,rungume take da wasu sabbin atamfofi wanda duk zuwa Nigeria sai an sayesu an tafi dasu,ayita ajiyarsu saboda tashin wata hidima ko kuma dinkin yaran gidan. Kusan al'ada ce da maina ya kafa saboda yadda ya tsani yawan ta'ammali da English wears da su sukeyi wanda ba komai bane kusan al'adarsu.
Ama ke biye da ita dauke da wasu kayan masu yawa itama data ware zata rabawa su najma,kayayyaki ne da tasan suna qanfarsu a can. Turus bibi tayi tana dan duban sultana
“Ya na ganki zaune kowa yana shiryawa?,bakisan tare zamu koma ba?,tunda shi hamidou komawarsu ba yanzun ba?” Idanu ta daga ta kalli bibi,sai kuma ta maida dubanta ga ama kafin ta janye duban nata idanun nata na cika da hawaye duk da basukai ga zubowa ba. Sam batajin zata iya komawa cikin qasar nijer taci gaba da rayuwa,a yanzun bata sha’awar hakan sam sam sam. Da wanne ido zata kalli jama’ar data sani a baya?,da wanne ido zata kalli mutane?,tace musu me?,batajin tana da rufin asirin da ya wuce mata rayuwa yanzu cikin Nigeria
“Zan zauna a nan ne,bazan biku ba” qarasawa bibi tayi ta zube kayan hannunta baki bude tana duban sultana
“Kamar yaya?,saboda me?” Hannu ta sanya ta dauke siririyar qwallar data ziraro mata
“Nafiso nan, nafison na zauna a nan kawai,ki barni a nan don Allah bibi” ta qarashe fadi muryarta tana rawa.
Baki buden bibi ta waiwaya tana duban ama,sai aman ta dagawa bibi hannu sannan ta tako kusa dasu
“Tunda hakan takeso kiyi haquri bibi ki barta a nan din,in sha Allah zanci gaba da kula da ita,zan kuma riqe amanarki,duk lokacin da taji zata iya komawa can din,zan shiryata na maida miki ita har gida in sha Allah” zama bibi tayi tana duban ama
“Yo na tafi a cuci wadannan bayin Allahn?,kina gani da idona ma ba wani nonon arziqi suke samu ba?” Da sauri ta dago kai tana duban bibi. Kaji wani sharri irin na bibi(sultana ta fadi a ranta),tun bayan abunma ba’a taba takurawa rayuwarta ba yadda bibin ke takura mata. Cikin dare zataje ta debo yaran,ta tasheta a bacci,haka zasu kwana jikinta,wani lokacin haka zata kwana tashinta wai ta basu nono,wani lokacin idan abun ya isheta saidai kawai ta sake mata kuka,ta maidata kamar wata saniya,amma yanzun cewa take ba nonon arziqi suke samu ba?.
Murmushi ama ta saki me sanyi,makauniyar qaunar da taga bibi na yiwa yaran mamaki take bata,yadda yaran suke da saurin shiga zukatan mutane ta sani wani abune kawai daga Allah
“Duk hakan ba zata faru ba in sha Allah,na miki alqawarin zan kula”
“Idan naga sabanin haka,ko nazo naga yaran nan sun zube fa ba zanwa kowa ta dadi ba” bibin ta fadi cikin salon mita
“Ba za’a yi hakan ba in sha Allah” ama ta sake tabbatarwa bibi.
A ranar dukkansu suka tarkata suka wuce,sai gidan ya zamana daga ama sai tanja da Bibi tace ta barwa aman ta tayata kula da 'yan biyu duk da gidan akwai ma'aikata sosai,sai aba sai kuma sultanan.
* Watansu hudu amma sunyi kubul kubul dasu kamar ana hurasu,ga nauyi da suka sakeyi saboda isashen nono da suke samu,tun sultanan najin wani banbarakwai idan tana shayar dasu,har ya zame mata tamkar wata hanya guda daya da zata samu kusanci da yaran,ta kuma qare musu kallo yadda take buqata,don bata wani sakewa ko cikakken kallo tayi musu gaban mutane koda kuwa ama ce.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
PAGE 29
Guraren tara da rabi na dare ya suka shigo gidan,yana jin sanda suka dawo gidan,yana zaune daha balcony din ama. Abinda ya qara masa takaici kowa da qafafunsa ya taka ya wuce ciki,amma ita sai da tanja ta rirriqeta saboda gajiya da bacci,ya dauke kansa yana jan tsaki sannan ya miqe yana sauka daga wajen.
****K’arfe sha biyu na rana ya fito daga sashensa,sunata shige da ficen tafiya kamun amarya anjima kadan. Wadanda ba’a yiwa qunshi ba su najma suna sassan bibi ana musu.
Falon ciki ya wuce ya zauna,sai bibi din ta fahimci kaman yanason yin magana ne da ita,don haka koda ta fito daga kitchen sai tabi bayansa.
“Meye da meye yau za’a yi a gidan oncle issoufou?”
“Kamun amarya ne yau din ai,da dare kuma su wuce dinner,shikenan an gama don gobe zasu wuce ghana da mijin,babu batun rakiyar amarya” kai ya jinjina
“Koda ba’a gama bama,bana buqatar SULTANA ta sake fita ko ina,bawai bikin gidan oncle issoufou kawai ba,kowacce unguwa ma daga yau,daga makaranta sai gida……..” Bai dire ba ihun kukanta ya ratsa gurin.
Sam bai ma kula tana wajen ba,ya waiwaya yana dubanta,shigowarta kenan sai ta watsar da abinda ta shigo dashi din ta shiga kuka da gaske kamar qanqanuwar yarinya.
“Wallahi sai naje Allah sai naje” ta dinga maimaitawa bakin fal da tsiwa da rashin kunya
Idanu ya zuba mata zuciyarsa tana tafasa,tabbas idan yaci gaba da zama a wajen zai mata mugun duka ne wataqila,kuma ama ta gargadeshi akan hakan,don haka sai ya miqe yana barin falon,amma cikin zuciyarsa yana tabbatarwa kansa tabbas yau zai mata gargadin da ba zata sake mararin maida masa magana ba.
Babu irin kukan da magiyar da bata yiwa bibi ba amma dukka suka taru suka bata haquri,tana kuka cikin falon bibi din tana jin tashin motocinsu suka fice suka barta,aka barta ita daya daga tanja sai deeja.
Da gudu ta diba tayi dakinta tana sake rusgar kuka,cikin zuciyarta fal tsana da haushin maina. Na meye zai hanata sakewa kaman kowa?,me ta tsare masa ne?,yabi ya damu rayuwarta cikin gidan sama da rayuwar kowanne mutum?. A duniya batajin akwai wani mutum data tsana sama da yaa maina a yanzu.
Tun tana kukan da sauti tanja na bata haquri har tanja dinma ta gaji,don bakinta kaman zaiyi ciwo,sai kuwa ta sauqaqe mata ta hanyar cewa
“Ki fitarmin daga dakina,ai harda ke aka kada baki,kuma wallahi bai isa ya hanani fita ba,ai ba ubana bane” ta fada da qarfi cikin zafin zuciya kaman tana gabansa. Juyawa kawai tanja din tayi tabar dakin,ta sani idan ranta ya baci komai ma zata iya fadi indai sultana ce.
K'arfe biyar saura na yamma ya dawo daga sallar la'asar da ya fita. Gidan ya dauki shiru,sai securities dake bakin aikinsu. Su dinma babu yawaitar kai kawonsu,saboda ganin yammaci ne,kuma babu yawaitar zirga zirgar al'umma cikin gidan bare unguwar da dama ba mutane ta cika ba.
Dakinshi ya koma ya aje wayoyinsa,sannan ya sake fitowa yana nufar sassan bibi da yayi imani zuwa yanxun bibi ta tsufa gidan biki.
Tun daga falon farko har na biyu ba kowa,sai na'urori dake ta faman aikinsu,ya kashe wasu ya wuce wasu har ya dangana da qofar dakin sultana,sai yadan dakata kadan,ya dage kaftan abaya dinsa ya zare belt din wandon jikinsa,sannan ya murza qofar dakin ya tura ya shige.
Tarwai dakin yake da haske,sai tarin ledojin madararta da Allah ne kadai yasan daga dare zuwa wunin yau guda nawa tasha. Yadda take bata muhimmanci sam abinci baya cikin tsarinta haka,da a rasa madararta gwara a daina girki a gidan ita a wajenta,komai nisan dare idan ta laluba babu ita to ko a ina taje sai an nemota,duk kuwa da cewa tafiyayya ce daga niamy ake jibge mata ita me tarin yawa.
Tana daga bari daya na gadon,kwance cikin kwanciyar rub da ciki wanda tayita ne daxu da tana kuka,daga kukan kuma ta zarce baccin. Hannunta daya ma ya sauko daga saman gadon,sumarta na barbaje saman filon,haka gajeriyar gown din jikinta ta tattare zuwa cinyoyinta.
Kadan yake ganin fuskarta,a hakan da take bacci zakayi tsammanin wata innocent ce,amma ba komai sai zallar fitsara rashin kunya da tarin raye raye da waqe waqe. Cikin ransa ya gama hango yadda zai firgitata,don haka ya matsa ya rage wutar dakin sannan ya tako a hankali ya tsaya a kanta.
Kamar wadda aka sanarma ko kuma taji cikin jikinta saita motsa kadan,tayi juyi zuwa hannun damanta dai dai sanda idanunta suka hango mata tsaiwarsa a gefen gado.
Razananniyar qara ta saki tana watstsakewa daga baccin ba tare data shirya ba. Ko gezau baiyi ba yana daga tsayen yana kallonta da lion eyes dinnanan nasa da suke da wani irin haske. Fuskarsa a dinke murtuk irin murtukewar da bata taba ganin makamanciyarta a tattare dashi ba.
Wani bugawa zuciyarta tayi bugun da ya kusa wucewa da numfashinta sanda zuciyarta ta raya mata wani abu,matsanancin tsoro rudu da firgici suka shigeta sanda tunaninta ya fara dawowa ta tuna cewa bibi fa bata nan,bama bibi ba,kowa na gidan baya nan,tana tunanin daga ita saishi
“Dalla malami ka fitarmin daga daki,kaga kowa baya nan ko?,to idanma FYADE kazo kayimin wallahi baka isa ba” ta fada da wani irin accent na zallar rashin kunya,rashin kunyar da take ganin itace kadai zat qwaceta
“Dalla malami?” Ya fada cikin tsananin bacin rai yana nufota
“Eh na fada din ba hak……” Bata sauke ba ya fidda hannu ya zabga mata mari. Qarar marin da a kunnuwanta suka tariyo mata kalaman wancan ‘yar sandar
“Eh ai dama kafin suyi aika aikarsu saisun mammare ‘ya’yan mutane sun bubbugesu da duka” maganar data tabbatar mata da gaske maina yazo ya aikata ne. Don haka tayi kukan kura ta miqe tsaye tsakiyar gadon ta fara ihun fadin
“Wayyo ku taimakeni,fyade zaiyimin,wai ba kowa?,tanja!…..tanja!”
“Shut up!” Ya fada da qarfi don tana neman cika masa kai da hayaniya ta kuma rudashi
“Wallahi bazanyi shuru ba,fyad……”
“Shut up stupid!” Ya kuma fada yana haurowa da zafin nama saman gadon. Kalmar fyaden idan ta fadeta yana jin kamar tana yankar zuciyarsa ne. Sai ya miqa hannunsa ya fincikota
“Shashasha mahaukaciya,bakisan fyade ba ko?,to zakisan yau me ake nufi da shi” ya furta yana ingizata saman gadon. Wani irin matsanancin fushi yakejin ya saukar masa,zuciyarsa na masa tariyar sanda ta fara jifansa da qazafin,yana jin idan ba maganinta yayi ya tabbatar mata da abinda kalmar ke nufi a aikace ba ba zata daina jifansa da mummunar kalmar ba.
Abinda yake shirin aikata matan bai sanya bakinta mutuwa ba,sai zagi data fara jifansa dashi ganin yana qoqarin rabata da gantalalliyar rigar jikinta. Yadda bakinta ya kasa mutuwa tsoro yaqi shigarta shi ya sake tunzurashi,ya kuma iza wutar fushin dake ruruwa a zuciyarsa. Sai kawai ya sanya mata dukka qarfinsa don ya nuna mata ya kuma TABBATAR mata da girman tazarar dake tsakaninsa da ita,ya fara yage rigar yana zubarwa. Nata qarfin ta sanya tana tunanin zata iya qwatar kanta dashi,saidai kuma inaaa.....wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa,ba abinda dan qarfinta ke iya tabuka mata. Sake tattaro qarfin nata tayi don masa waigi daga shiga wajen da ya nufa din tana kiran masa Allah ya isa,Allah ya isan da yakejin kamar ta watsa masa wuta,hakan ya tunzurashi ya sake saka mata Mari kuncin hagu da damanta,marin da ya sanya labbanta na qasa fashewa,ya kuma dauke mata wuta gaba daya,wutar da bata tashi dawo mata ba har sai da ya soma shiga katangaggen shingen da ko kusa ko alama ba'a tsammaci budeshi ba a irin wannan lokacin.
Azababbiyar azabar da ta zarta ta marukan da tasha a hannunsa ya ratsata,tun daga tafukan qaffaunta har tsakiyar qwaqwalwarta. Kumburarrun idanunta da sukayi kwanciyar jini ta gefansu ta rintse tana jin numfashinta yana barazanar barin gangar jikinta a hankali,saidai duk da haka bakinta bai fasa fadin muggan kalamai a kansa ba,zuciya cike da tsana,gangar jikinta bata gaza ba tana qoqarin ganin ta dakatar dashi da sauran qarfin da takejin tana dashi har zuwa sanda ruhi da gangar jikinta suka gaza daukar lalurar maina,suka kuma gaza daukar girman nauyin da ya azawa qananun shekarunta numfashinta ya fara fusga a hankali,dukka kalamanta suka gaza,idanunta da ganinsu ya raunata ainun suka rufe,bakinta kuma yayi shuru kamar yadda numfashinta ya fice fit daga gangar jikinta,komai nata kuma ya tsaya cak,wanda duka wannnan maina bai lura dashi ba.
Wani irin abu da bai taba kwatanta jinsa cikin jikinsa ba yaji yana ratsashi,wani irin yanayi da bai taba cin karo da kwatankwacinsa ba,daga gangar jikinsa har zuciyarsa wasu mabanbantan al'amura ne ke tarayya cikin kowannensu,jikin da kuma zuciyar. Yayi wani ficewa daga hayyacinsa,fitar hayyacin da ta sanya yayi wata mummunar barna,wadda bai ankara ba sai bayan shudewar wani zamani.
Ya zare jikinsa daga na sultanan,hankalinsa da nutsuwarsa suna dawo masa sannu a hankali. Wani mummunan firgici ya tsinci kansa a ciki sanda ya dafa hannuwansa saman gadon ya jisu cikin damshi ainun. Koda ya duba sai yaga kalar ja,jar kalar dake alamta masa lalllai jini ne,jini kuma me yawan da ya sukurkuta masa tunani
“Jini?,daga jikin wa?” Ya fada muryarsa na wani irin rawa. Da mugun hanzari ya yaye dan blanket din da ya rufe sultana dashi,a nan ya samu ainihin amsar tambayarsa.
“Sultana!” Ya kirayi sunanta da wata razananniyar murya. Dukka hannunsan ya sanya ya dagota yana duban fuskarta.
Kowacce halitta dake fuskarta ta sauya kamar yadda gangar jikinta ya saki gaba daya. Ba wani abu dake motsi a jikinta,saima sandarewa da yaga tayi. Hancinsa da ma bakinsa yakai ga fuskarta,ba numfashi ba alamarsa,sai sanyi da fuskartata da kuma tafukan hannayenta sukayi.
“Ta mutu!” Ya fada a gigice bayan ya sanya yatsunsa biyu a jijiyar daya tabbatar a karatunsu muddin bata harbawa to batun rayuwa a tare da mutum
“Sultana!” Ya sake kiran sunanta wanda ya taho hade da gunjin kuka.
Kansa ya kifa saman tata fuskar ya saki kuka me qarfi,kukan da tsahon rayuwarsa bai taba yin irinsa,ya kashe musu sultana,da wanne ido xai kalli bibi?,da wanne ido zai kalli aba?,uwa uba da wanne ido zai kalli nafessa?. Ya kashe sultanar da ya raineta da hannunsa?,ya kashe sultanar da yaci kashi da fitsarinta?,da wanne ido zai kalli sauran mutane?.
D'il yaji harbawar jijiyar sau daya,abinda ya sanyashi daga kansa da sauri yana dubanta,ya kuma tattara dukka hanakalinsa da nutsuwarsa ko zai sakejin ta harba din amma bata harba ba. Hannunsa ya sanya ya dafe saitin zuciyarsa da qarfi wani kuka me ciwo yana sake qwace masa. Da sauri ya sauka daga gadon ya gyara mata kwanciyarta.
Cikin mintuna goma ya bata dukkan wani tallafi da zai iya sanyawa ta rayu,saidai bata dai bada wani reaction ba har ya gama. Amma kuma yana da cikakken hope akan taimakon da ya baiwa numfashinta da zuciyarta,Sai ya tattara komai nasa ya sake matsawa gabanta ya shafa sumarta yana jin kamar zuciyarsa zata fado.
Bazai iya tsaiwa yayi ido hudu da Bibi ba
Bazai iya fuskantar aba ba
Me zai cewa ama?. Sai ya sauke hannunsa da sauri ya juya yana fita daga dakin,wanda daga nan bai zarce ko ina ba sai dakinsa.
Ko minti biyar bai rufa ba a dakin ya fito,babu komai a hannunsa sai qaramar takarda daya soketa jikin qofar dakin nasa,sai wata qaramar jaka dake riqe a daya hannun nasa. Ya fara takawa yana barin ainihin ginin gidan yana dosar qofar fita a gidan. Zuciyarsa na wani irin fusgarsa,wata izuwa dawowa cikin gidan,wata kuma zuwa fita daga gidan,fita kuma da zata kawo nisan tazara me yawa,har sai ya tanadi amsoshin da zai baiwa ahalin MAYAK’I. walau SULTANA ta rayu ko kuma TA RASA RANTA,Ya tabbatar dole wataran ya fuskancesu,dole ya fuskanci abinda ya aikata a yanzun,saidai kuma a yanzunne bai shirya fuskantarsu ba.
SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIKA,ASH HADU AN LA’ILAHA ILLA ANTA,ASTAGFIRUKA WA’ATUBU ILAIKA
MA’ASSALAM👑👑
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 30
“Yaran ummin aneesan fa?,suma ba kano din suke tafiya ba?,don Allah aba kada ka hana,kada kuma ka bari ta gane zucoyarka tayi rawa akan al’amarin,muna da buqatar mu.maida sultana ainihin mutum,aikin da maina ya gagara yi inaso na aiwatar masa,koda baya raye na tabbatar hakan zai bashi sukuni cikin kushewarsa” ta qarasa fada zuciyarta na yin wani irin nauyi. Shuru yayi tun daga lokacin bai sake cewa komai ko ya nuna baiso din ba,hasalima da dukka kudinsa ya bayar akayi komai daya dace,itakam sultanan ma batasan meke faruwa ba,don rayuwar kebe kai tafi komai yi mata dadi a yanzun,sai ayi abu cikin gidan sau babu adadi amma bata sani ba.
K'arfe tara na dare ta tura qofar dakin sultana din ta shigo. A lokacin benazeer na rungume a kafadarta tana taba rigima,batoul na cinyar aba tana bacci,don ita din ba kasafai ta fiya rigima ba.
Da shanyayyun fararen idanunta ta waiwayo tana duban ama,kafin ta janye idanun nata ta dorasu akan benazeer da aman ta kwantar mata saman gadon,sai kuma ta dauke duban nata daga kan benazeer din ta sake maidawa fuskar ama
“Hala shirin kwanciya kikeyi?” Ama ta tambaya tana sake qarema sultanan kallo. Ta sauya sosai,har yanzun dai batayi qiba ba,amma jikinta yayi kyau kai sai ka rantse bata taba sanin d’a namiji ba bare ayi zancan haihuwar ‘yan biyu,wannan kyawun nata ya sake fita da wani irin sirri na cikar cikakkiyar mace,idanunta sun sake girma da haske,hatta da idonta dayan da ya samu dan matsalar da sai ta sanya masa glass babu lallai kai ka fahimci hakan saboda yadda suma suka bude fes dasu kaman dayan. Gashinta ya wani sake cika kamar kowacce gaba ta jikinta ke fara nuna girma na asali bawai girman da samuwar ciki ya tilasta zuwansa ba.
“Eh ama” ta amsa mata tana bude man shafawarta sannan ta koma ta zauna saboda ta fahimci da magana ama din ta shigo.
“Ya kamata,sultana”
“Na’am ama” ta amsa mata a sanyaye tana fatan ba wani sabon abu bane kuma ya taso
“Kinsan rayuwa babu abinda yakai ilimi dadi da daraja,babu kuma abinda yakai ilimi maidaka cikakken mutum haka ne?” Kai ta gyada a sanyaye karo na biyu
“Mun yanke shawara,in sha Allah nan da sati biyu masu zuwa tare zaku wuce kano tare da yaran ummin aneesa,zaki fara makarantarsu,saidai mun roqi alfarmar koda daga j.s3 ne idan hakan ta samu” ama ta qarashe fadi tana zubawa sultana idanu. Kai ta jinjina,ita a yanzun batajin akwai wani abun da zai taba mata zuciya,ko ya sosa mata rai,batajin akwai wata tsana ta wani abu cikin zuciyarta da zatayi girman tasirin wutar tsana da qiyayyar dake ruruwa yanzu haka a zuciyarta
“Allah ya kaimu” sultanan ta fadi a sauqaqe kai tsaye kuma ba tare da taji komai cikin zuciyarta game da batun ba. Sake kiran sunanta ama tayi a karo na biyu,sai ta kuma amsawa tana duban ama
“Ki daure kiyi karatu sultana,banason wadanda suka sanki a shekarun baya su sake ganinki dai still yadda kike,ba wani ci gaba,babu kuma abinda ya canza daga gareki” murmushin qasan zuciya ne ya subuce mata,tadan murmusa ta yadda ita kanta ama din ba zata gani ba,ita wai meye ya ragewa rayuwarta?,bata da MANUFA burika da fata na rayuwarta dukka sun jima da bizne kansu cikin qarqashin duk wani buqatu na rayuwarta gaba daya.
*K’arfe takwas na safiya suna qofar gidan ama,yaran ummin aneesa da suka kasance ‘yammata kamarta a shekaru ne. Anata zuba kayansu cikin mota,sunata kuma kai da kawowa cikin ‘yar hargowa da rigingimu nasu irin na sako da sako.
Daga gefe daya sultana na tsaye kawai,jingine jikin motar. Sanye take da uniform da yayi matuqar karbarta ainun,idanunta saye cikin farar kwalbar glass wanda ya zame mata tamkar ado,ba zaka taba tunanin lalurar idanu bane suka sanyata sakasu,sun amsheta ainun,sun kuma qarawa zagayayyun idanunta wani irin kyau da kuma kwarjini matuqa.
Sai da aka gama komai tas sannan ta buda motar ta shiga,ama ta shiga gaba dauke da BATOUL, goumar ya buda gidan baya dauke da BENAZEER yanata cakularta da wasa tana qyaqyacewa da dariya. Shigowarsa gefanta ya sanyata daga shanyyun kewayayyun idanunta ta kalleshi dasu. Kusan tare suka kalli juna,wannan yayi sanadiyyar haduwar idanunsu guri guda.
Hasken fararen idanunta ya dakeshi sosai,yayi saurin zare idanunsa shima yana ci gaba da tsokanar benazeer suna sake cikawa sultana kunne. Basu kuma bar kunnuwannata sun huta ba har suka isa airport. Wannan karon su aneesa nata murna,sun huta dogon zaman mota daga abuja zuwa kano,tafiyar jirgi ce cikin mintuna qalilan zasu isa.
Basu kuwa dauki lokaci ba,duka duka mintuna qalilan suka sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na malam aminu kano,daga can din kuma suka samu daya daga cikin motocin dake zirga zirga cikin airport din ta daukesu zuwa HASSAN IBRAHIM GWARZO.
**Motoci da dalibai fal qofan makarantar. A irin wannan lokacin akan samu cikowar mutane irin haka da ababen hawa.
Cikin lokaci qalilan suka isa office na shugaban makarantar,ama tayi dukkan abinda ya dace goumar yana tsaye yana rungume da twins. Daga goumar din sai ama,su biyun kacal sukafi sakewa dasu fiye da kowa,sun gane goumar sosai kamar yadda suka gane ama din.
Tattaki suka yima sultana har zuwa hanyar da zata sadata da bangaren mata. Iya ama da su benazeer,don goumar tun daga can mararrabar section din maza da na mata suka dakatar dashi. Haka tsarinsu yake,kome alaqarka da mutum ba zasu tabi bare ya tsallake wannan shingen ba muddin ba section din jinsinka bane.
“Allah ya bada sa’ar karatu sultana,shikenan sai munzo visiting?” Ama ta fadi tana duban fuskarta. A sanyaye ta daga kai ba tare data dubi ama ba,hankalinta yana rarrabuwa akan yadda rayuwa zatazo mata cikin makarantar. Ta gani komai da ama ta shigar ta shigar dashi ne dai dai da na kowacce yarinya matashiya budurwa.
“Shikenan,Allah ya bamu alkhairi” ama ta sake fadi,sai sultana din ta kuma jinjina kai kana ta fara taku daya biyu zata wuce ciki,saidai kuma batasan dalili ba,can qasan zuciyarta takejin wani irin nauyi yana mamayarta,kamar akwai abinda takeson aiwatarwa,kamar akwai abinda zuciyartata keso wanda ta gaza yi mata shi.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 31
"sultana" taji sautin muryar ama na kiranta. Waiwayowa tayi suka hada idanu,a hankali sai ta sauke idanunta akan batoul da benazeer. Sauko da batoul din ama tayi ta miqa mata ita,takowa tayi a hankali ta qaraso gaban ama din,hannayenta ta sanya duka biyun ta karbeta. A hankali ta dora idanunta saman fuskarta, fuskokinsu suka gauraya waje daya,sai yarinyar ta sakar mata dariya tana qoqarin kamo eye glasses dinta. Batasan ya akayi ba saita tsinci kanta da sakin wani siririn murmushi,ta saka nata hannun ta riqe dan qaramin hannunta. Daidai lokacin benazeer ta fara gwaranci.
Sake daga kai tayi ta kalli benazeer din,hannu take miqa mata tana zillo kamar zata fado,maida BATOUL tayi daya side din ta amshi benazeer,sai ta hadasu dukka su biyun ta rungumesu a qirjinta ba tare data shiryawa hakan ba. Luf sukayi daga ita har su,yaran sunyi shuru cikin qirjinta kamar wadanda sukasan meke shirin faruwa,kamar wadanda sukasan tana shirin yin nesa dasu ne har na tsahon watanni uku. Cikin qirjinta taji zuciyarta tana bugawa da kyau,sai ta maida idanunta kawai ta lumshe.
Idanun itama ama ta lumshe tana jin wani yanayi yana sauka a zuciyarta,tsakanin uwa da d'a sai rabbussamawati,koda kuwa dan na shege ne muddin akwai zuciya a qirjin uwar. Ta bude idanunta sanda sultana ke miqa mata su,sai dukkansu suka riqe gaban hijabin sultana din suna qyuyar sauka. Murmushi hade da hawaye ne suka subuce ma ama din,hakanan sultanar itama hawayen ne maqale a kuncinta. Cikin dabara da waqar da ama keyi musu ta samu ta amsosu,saidai har suka bar wajen idanuwansu da hankulansu yana kan mamarsu.
Ta shiga dakinsu,ta kuma sameshi cikin tsafta da tsari. Yanayin dakunan da yadda ta samu daliban ciki kawai ya soma gaya mata inda tazo din waje ne na tarbiyya,waje ne na cikakken karatu,waje ne kuma bana wasa ba. Kintsattsun matasa kamarta,kowacce ta karbeta hannu bibbiyu,hakanan itama tayi iyakar bakin qoqarinta a ranar tata ta farko ta sake musu an gaisa da kyau,daga nan kuma ta kama kanta ta soma sabgogin gabanta da qoqarin fahimtar komai.
3:45 am
Tsakiyar baccin da bai jima da daukarta ba saboda tsananin tunanin da har yau batasan meye qarshe da mafitarsa ba taji ana tashinta cikin nutsuwa. A hankali ta buda idanunta tana qarewa dakin kallo, tunaninta ya dawo fes yana tuna mata a inda take din a yanzun. MAKARANTA kwanyarta ta tuna mata.
Gefan da ake tabata din ta waiwaya. Tana zaune riqe da uniform dinta a hannu tana kallonta,fuskarta qunshe da murmushi. Fatima ahmad yusuf idan bata manta ba shine kiran data kirayi kanta dashi sanda suke gabatar da junansu. Kusan tafi kowa kusa da ita ita da ameena aleeyu dake maqwafataka da ita ta hannun hagunta.
“Ki tashi,lokacin sallar asuba ya kusa,mu samu mu gama komai a nutse kafin captain ta fara counting” ta fadi mata tana ci gaba da harhada abubuwan da zata dauka. Idanu da baki sultana ta saki tana kallonta,saita maida dubanta ga qaramin agogon dake dakin. Sallar asubahin tun yanzu?, counting na meye za’a fara?. Bata ida wannan tunanin ba taga shigowar ameena aleeyu tsaf cikin uniform. Binta tayi da kallon mamaki,ko hudu na dare bai cika ba? ,A wannan daren me kuma sukeyi su din haka?.
“Qarasa muje muyi alwala da wuri kada mu samu cinkoso muyi shigen ta jiya” ameena ta fada tana zama sanya hijabinta sannan tace
“Kin tashi lafiya sultana?,mamaki nasan kikeyi ko?,dukkanmu haka mukayi kaman naki dinnan farkon zuwanmu makaranta,dole kowanne daliba ya tashi da wuri yaje yayi alwala ya wuce masallaci sallar asuba,muddin ka makara kuma…..hmmm akwai qura,ni da fatima ba zamu iya tuna randa muka makara din ba,saboda muna cikin dalibai masu kiyayewa” kai ta jinjina tana sake binsu da kallo kamar baqin halitta,kawai saita juya a hankali ta maida kanta ta kwanta tana lumshe idanuwanta hadi da cewa
“Kuje zan taho” tare suka juyo gareta
“Karkiyi haka,da zaki taso mu wuce zaifi fa” kanta ciwo yake sosai,don ko baccin awa biyu cikakke batayi ba,runtse idanun ta sakeyi tana jin kamar damunta kawai sukeson yi
“Kuje kawai karku damu” shuru sukayi na wani lokaci suna duban juna,saboda sunsan horon da takeson jefa kanta din ba mai dadi bane,abune da kowanne dalibi cikin makarantar ke qoqarin kaucewa. To amma ba yadda suka iya kasancewar dukkansu ba masu son shishshigi ko hayaniya bane sai suka qyaleta.
Duk da baccin bai dawo ya dauketa ba gaba daya amma ya soma fusgarta ta soma jin hayaniya sama sama,kowacce daliba tana tashi gami da kwasar uniform dinta a gurguje tana sanyawa. Idanunta ta qarasa budewa tsaf sanda wata kakkaifar murya ta soma fadin
“One……two…… Three……” Jin kamar ana guje guje ya sanyata bude idanun nata. Dakin duka ya hargitse,kowa takai takai yakeyi wajen qoqarin saka uniform sannan kuma ya fice da gaggawa kafin a kammala qirgen. Haka kawai tsoro ya dirar mata,ta sauko da sauri cikin firgicin wanne abune me muni zai iya samunta idan suka fice suka barta a nan,sai ta lalubi hijabinta ta zura tabi bayansu ba tare data tsaya sanya uniform ba.
Da gudu gudu wasu ke nufar gate dinsu na farko,tun kafin su isa ta jiyo shigen wancan muryar tana counting itama,saidai dab da zasu isa me lissafawan taja qofar ta bame,sai gani sultana tayi dalibai suna zubewa bisa gwiwoyinsu hadi da furta
“Astagfirullah……. astagfirullah” cikin wani irin tashin hankali. Abun ya bata tsoro ya kuma daure mata kai,bata da zabi illa itama tabi sahunsu ta zube a wajen. Sai da suka gama neman gafara sannan suka zarce wajen daura alwala. Tasha wahalar kafin ta samu kan famfo din da zata daura alwalar,abinda nan duniya bata taba saninsa ba baya ga abinda ya faru da ita ba wato wahala wajen samun wani abu na duniya. Tana alwalar tana tuna adadin yawan kan famfo dake gidansu,wanda hatta tsuntsayen dake gittawa ta cikin gidan sai a inda suka zaba suke shan ruwa ballantana su,su dinma ita sultana shalelen bibi da aba.
Ayarin ta sake bi suna nufar wani guri,bata karanci ina bane sai da suka qaraso,masallaci ne,shima anja gate din an rufe,dukkansu saida suka sake zaman yin istigfari sannan aka bude musu suka sanya kai ciki.
Cikin wani irin tsari da burgewa kowa yahau sahun sallah,aka kabbara sallah. Mintuna kusan takwas sannan aka idar,tana niyyar miqewa taga ba wanda ya motsa sai qur'anai da ake budewa,kowa kuma yana lalubar 'yan ajinsu. Idanu ta shiga budewa tana waige waige,ba inda ta sani,ba kuma wanda take ganewa a wajen. Cikin haka Allah ya taimaketa ta hango fatima tana daga mata hannu. A sanyaye ta isa kusa dasu,ta miqa mata qur'anin,tasa hannu biyu ta karba,ta samu waje kusa da ita ta zauna.
“Ki bude,recitation za’ayi,za’a yi mana qarin karatu kuma,sai qarfe bakwai sannan zamu koma hostel mu shirya shiga aji” kai ta jinjina qasan zuciyarta fal da mamaki,wacce irin makaranta ce ama ta kawota haka?.
Buda qur'anin kawai tayi ta zuba masa idanu,saboda inda ake musun ita sam batazo wajen ba,yo inama tayi jumurin zuwa makarantar ballantana ta kawo nan,ta sani dai,ta kuma tabbatar su aminata da suke aji daya tare a baya sun wuce haka yanzun,saboda makarantar islmiyyarsu badai karatu ba,ita dince dai da bata sanya aka ba.
Tana nan zaune aka gama biyawa aka soma karanta musu suna bi,duk sai taji ta muzanta,bata kuma ji dadi ba ganin kowa yana bi tar tar,ita kadai ke baza idanu. Kusan ita daya ce sabuwar daliba cikinsu,saboda dokan makarantar bata yarda da daukan dalibi daga kowanne mataki ba saidai matakin farko wato J.s one,ita dinma sa'a ta taka da kuma sanayya ya sanya suka kaita j.s3 din.
Har akayi aka gama bata iya kama komai ba a ciki. Hakanan taji jikinta yayi sanyi qwarai,irin sanyin da bata taba ji ba wai akan karatu,ko don wannan din wani littafi ne na daban?,na musamman da ya banbanta da dukka sauran litattafai a duniya.
Suna hanya ameena aleeyu da Fatima ahmad yusuf sunata hirarrakinsu,saidai abinda ta fuskanta a gurguje kowa ke yin tafiyar zuwa hostel. Tun tana binsu a hankali ta fuskanci zasu tsere mata don haka ta dan daga qafa ta taddosu.
Waiwayota ameena aleeyu tayi tana murmushi
“Saikin saba da dukka tsari da dokar makarantar nan sannan zaki zauna lafiya,yanzun zamu wuce hostel ne,ayi share share,sannan mu wuce kitchen yin breakfast” idanunta tadan fiddo,duk wannan wahalar da tayi,da kuma qoqarin da take ta koma ta wuce toilet ta sheqa wanka ake batun shara da cin abinci?.
“Wanka kuma fa?” Ta tambaya tana dubansu. Dariya kadan sukayi
“Ba batunsa,sai Allah ya kaimu biyu na rana idan an tashi class” cikin ranta takejin ba zata iya wannan rayuwar ba,itakam koma meye dole tayi wanka da safen kafin ta wuce aji,don ba haka ta saba ba.
Suna isa labour perfect na raba aiki,kusan kowanne class da suke hade a hostel guda sunsan area din da zasu share,suna da yawan da ba'a kula da baquwar fuska bace ita,don haka ta nufi bangaren da toilets dinsu yake don yin wankan. Kowanne toilet a kulle yake gam,taja baya ta tsaya tana duban qofofin,ta kuma kalli bucket din hannunta. Da gaske kenan saidai ta koma sai qarfe biyun kamar yadda ameena aleeyu ta gaya mata. Ranta a bace take takawa zuwa sassan dakinsu cikin babban compound na hostel din nasu da yakai girman babban parking space,bayan football field da suke dashi dake hade da table tennis.
“Ke!” Taji an kirata daga bayanta. Cak ta tsaya tana jin amsa kuwwar kiran cikin kunnenta,irin kiran data fi tsana duk duniya,kiran wulaqanci da yaa maina kadai keyi mata shi,a yanzun batasan kuma waye ya ara ya yafa ba. Waiwayawa tayi jin an sake ambatar
“Ba dake nake ba?” Kafin tayi komai taga daya daga cikin daliban dake daura dasu ta saki tsintsiyar hannunta,ta kuma qarasa da sauri ta zube bisa gwiwoyinta tana fadin
“Aunty gani”. Mamaki sosai ya kama sultana,aunty kuma?,harda duqawa saman qafafu?,ita sam a wannan wajen bataga aunty ba,tunda duka duka ma autyn da ake kira dinma baifi ta bata tazarar shekara biyu ba
“Ba dake nake ba,da wannan ‘yar iskar nake” ta fadi cikin dagawa da izza tana nuna sultana. Wani abune yazowa sultana wuya ya tsaya mata,ta tattara dukka miyan bakinta ta hadiye,ranta yana sosuwa da sunan ‘yar iska data kirata dashi. Waishin ma ita din wace da zata kirata da wannan sunan?,ta buda baki zatayi magana muryar Fatima ahmad ya gauraye gurin
“Baquwa ce aunty,don Allah batasan tsarin komai ba,tana cikin sabbin daliban da aka kawo jiya”
“Tambayarki nayi?,ita batasan wacce makaranta ta shigo ba?,uban meye takeyi da botiki a hannunta lokacin tsafta da gyara waje?”
“Bata sani ba kiyi haquri aunty”
“Samomin bulala” prefect din ta fadi tana bawa yarinyar dake durqushe a gabanta umarni.
Tsaiwa cak sultana tayi tana jiran ganin ikon Allah,tanason ganin yau din wacece zata daketa?,wacce me tsautsayin ce?,batasan babu wani halitta da ya isa ya daketa ba bayan ruwan sama?. Cikin qasa da minti daya yarinyar ta iso,cikin ladabi irin nasu na makarantar daya zamewa kowanne dalibi tilas ya siffantu dashi ta duqa ta miqa mata
“Zo nan” ta yiwa sultana umarni cikin tsawa
“Kije don Allah,don Allah kije sultana” Fatima ke fadi cikin tsoro
“Har saikin roqeta ma?,idan batazo bama zan qaraso da kaina” perfect din ta furta tana takowa gurin sultana din cikin izza,zuciyarta na gaya mata duk yadda akayi ‘yar gidan uban wani ne daga wata qasar,don sam batayi zubin qabilun nigeria ba
“Durqusa kikayi tsai kina qarewa mutane kallo!” Ta fadi cikin wata sabuwar tsawar
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 32
Ci gaba da duban tsakiyar idanunta sultana din tayi tana hadiye wani abu daya tsaya mata a maqoshi,wannan din ya sake tunzura prefect din,ta daga bulalar hannunta da nufin saukewa sultanan
“Lafiya?,me kukeyi a nan carko carko?” Muryar Metrom din dake kula da shiyyar ta gauraye wajen.
Cikin fushi perfect din ke maida jawabi,gurin yayi tsit har ta gama
“Shikenan ya isa,kowa ya koma kan aikinsa,ke kuma huda kiyi haquri,baquwa ce,amma zan mata bayanin komai” wani irin tsuka wadda aka kira da hudan taja,alamu dake nuna takaicin dake ranta fal,don taci buri sosai na ladabtar da sultana. Kyawunta wani abune da ya bugi zuciyarta qwarai ya kuma sanyata kishi.
Idanunta da suka dan jirkita ta lumshe sannan kuma ta budesu,ita kanta taso yarinyar da aka kira huda ta samu isowa gareta,ba shakka da ta barwa rayuwarta darasi. Don rayuwa ta cimmata hakan bai nufin komai da komai daga asalin sultana ya sauya ba,ba zata lamunci cin zarafi ko kuma qasqanci ba.
“Taho muje” taji muryar Metrom din na fadi tana kama bucket din hannunta. Bata musa ba tabi bayanta har zuwa wani kebantaccen waje da Metron din kan zauna ko tayi ajiye ajiyen kayanta
“Zauna,sultana mayak’i ko?” Ido ta daga ta dubeta tana mamakin yadda ta kama sunanta haka kai tsaye kuma lokaci guda.
“Zauna” ta sake maimaitawa,ba musu ta samu waje ta zauna,itama Metron din ta zauna tana duban idonta
“Sunana maama asabe,kina iya kira na maama ko asabe,da farko inason shaida miki,duk wani da kk da buqata ko menene shi kina iya shaidamin kai tsaye,za kuma ki sameshi in sha Allah” saita tsagaita tana kallonta. Mamakin sultana ya sake qaruwa,to meye hadi ko alaqarta da ita bayan yau ne ita karo na farko a rayuwarta ma data fara ganinta,ta yaya zata buqaci wani abu a wajen ma’aikaciyar da idan ita sultanan bata taimaketa ba ita din ba zata taimaketa ba
“Kada kiji shakkar nema ko tambayar komai daga hannuna tamkar kina gida,don komai zai fito daga hannuna da zaki buqata din daga gidan yake…..makarantar nan tana da dokoki da qa’idoji masu tarin yawa,duk dalibin da kika gani a makarantar nan yana rayuwa ne a kansu,kina da wata kariya da alfarmar da ba lallai ki fahimci abinda zan ce ba,kawaidai abinda zan gaya miki shine,don Allah ki koyi kiyaye kowacce doka da qa’ida,ta yadda babu wani hukunci da zaya dinga hawa kanki,ni kuma zanyi dukka qoqarina wajen tafi da komai” shuru tayi tana jujjuya maganganun maama asabe dake tafe da wani irin surkullen zance data kasa fahimta,to wai shin maama asabe ta santa ne ko kuwa?,akwai harshen damo cikin maganganunta da bata fahimci ina ta sanya gaba ba,daga qarshe kawai ta yanke ta gyada mata kanta
“Yauwa,yanzu lokacin tafiya kitchen yayi,kibi ‘yan uwanki ku wuce” kai ta sake gyada mata,sannan ta miqe riqe da bucket dinta.
Cikin uniform ba tare da wanka ba ta sami su fatima,ta lura da tuni sun saba da wannan yanayin,don shirin tafiya kawai sukeyi kitchen. Ameena ce ta kama hannunta
“Don Allah ki kiyaye sultana,haka makarantar take,amma muddin kika kiyaye zaki fahimci rayuwa ce me dadi kike kai” bata ce da ameena komai ba,ta sunkuya qasan gadonta ta sauya takalminta. Wani irin takalmi ne me azabar tsada da kaf fadin makarantar…..duk kuwa da kasancewarta makarantar yaran masu hannu da shuni za’a samu me irinsa,ta dauki school bag dinta da tuntuni take dauke da litattafanta a tsare ta goya sannan tabi su fatima suka wuce kitchen.
Babban hall ne da aka tsarashi da table da kuma kujerun cin abinci rukuni rukuni,kowanne rukunin table yana dauke da kujerun zama guda goma,kaman yadda yake a doka mutum goma ne ke zama kowanne table. Kafin isowarsu an shirya kowanne table da cooler din abinci, spoon cups da plates da kowanne dalibi zai buqata.
Yadda taga kowa ya zauna haka itama ta zauna,ta dinga nazarin wajen da.idanu tare da cika da mamaki,mamakin yadda duk yawansu kowanne dalibi na zaune bisa kujerarsa cikin tsari,kowanne table kuma cups da sauran tarkacen kai a qididdige suke dai dai da yawan masu zama a wajen.
Fatima ce ta miqe tayi saving nasu kamar yadda kowanne table mutum daya ke wakiltarsu. Tabi plate dinta da kallo sanda fatima ta gama ta koma ta zauna. Doya ce da qwai,sai kuma tea lafiyayye cikin kowanne cup,ta dauke idanunta ta fara bazashi a hall din sanda taji sun rude da addu'a duka lokaci guda.
Addu'ar cin abinci ne,sai da suka sauke sannan kowa ya fara kaima cikinsu,a sannan hayaniya ta rude a wajen. Ko hannu batakai ta taba abincin ba,bawai don baiyi.mata bane ba,aah tsabar rashin sabo da cin abinci cikin gamayya haka,uwa uba kuma a gida ta saba,baa taba ajjiye musu breakfast qwaya daya tsura haka,a qalla akwai kalolin breakfast uku ake ajewa ka zabi son ranka.
“Minti talatin kacal ake bayarwa,kiyi ki fara ci kafin a fara counting” ameena aleeyu ta fada tana kai cup din tea din bakinta.
Tun asali a dabi'arta bata iya sauri wajen cin abinci ba,don haka tana tsaka da soma ci din taji an fara irge kwatankwacin irgen da taji anyi dazu da asuba wanda ya sanyasu zubewa suna istigfari. Ture abincin tayi sanda fatima ke gaya mata lokaci ya kusa cika,gaba daya abincin ya taru ya dunqule mata a qirji,ta sunkuya ta dauki handbag dinta
“Baki dauki ruwanki ba” fatima tace da ita,kai ta girgiza alamun AA tana yin gaba,hakan bai hana Fatima daukan sassanyan ruwan ba tabi bayan sultana din dashi,tausayin sultanan yana kamata, saboda ta sani bata saba da irin rayuwar bane bisa dukkan alamu. Kaman hakan suma suka fara,sai gashi yau rayuwa ta fara koya musu yadda zasu rayu cikin dadi da kuma akasin hakan,hakan kuma ya zame musu jiki tamkar dama a haka rayuwar tasu ta taso.
Sai da taji qishirwa da gasken gaske,ta kuma tabbatar babu wani sauran bottle water a nan wanda ta saba sha a gida sannan ta amsa daga wajen fatima ta sha.
Kusan duk karatun da akayi cikin ajin shima nata idanu,bata fahimtar inda komai ya dosa,bata gane komai,tana jina rayuwarta kamar bata taba zama a aji ba. Haka kawai sai taji ta muzanta,ta kuma tsargu,kowa yana karsashi tare da qoqarin bada gwargwadon fahimtarsa cikin aji amma banda ita. A hankali ta dinga jin wani abu me kama da rashin jin dadi yana sauka a zuciyarta,ta dinga jin me ya hau kanta wancan lokacin?,me yasa bata tsaya tayi karatu ba?,tana gani yanzu a gaban idanunta tamkar ita daya ce bata gane komai cikin ajin. Koda kuwa akwai banbancij harshe da yare a tsakaninsu,amma tayi imanin inda ta tsaya tayi karatu a baya ayanzun batajin akwai abinda zaya gagareta,tunda ko a makarantar tasu ana koyar dasu harshen turanci sosai,kuma kaf gidan ba wanda ba zaya iya jefa maka turanci ba,bare larabci da ya zama yaren dukkan musulmin duniya.
Sha daya aka fita break,masu sha'awar cin provision dinsu suka diba sukaci,ciki harda su fatima data fahimci ita da ameena aleeyu komai nasu a hade yake. Sukayi sukayi tazo suci abinci amma ta qiya,don bata sha'awar cin komai,hasalima dandanon bakinta ya dauke,ba abinda ke kai kawo a kwanyarta illa yadda zata tafiyar da baquwar rayuwar data fado mata rana tsaka ba tare data shirya ba.
Biyu na rana aka tashi da classes. Tana kallon yadda dalibai keta walwala zuwa masallaci,kowa na sabgar gabansa,sai ta dinga jin inama ace itama tana daya daga cikinsu. A yanzu kawai tana jin gangar jikinta da ruhinta ne a wata baquwar duniyar,bawai irin duniyar data saba rayuwa a ciki ba.
Sallah sukayi bisa jam'i a masallacin mata,abinda kaf rayuwarta zata iya cewa bata taba yi ba wato sallah cikin jam'i. Ta saba kammala sallarta a mintuna qalilan,yau sai gashi itace da tsaiwar sallah,sannan kuma bayan an idar sukayi zaman yi azkar na bayan kowacce sallar farilla,nan ma 'yar kallo ta zama,ta lumshe idanunta muryoyin daliban cikin NISHADI suna jeranta addu'o'in na shiga cikin kunnenta. A hankali ta dinga jin wani sanyi yana saukar mata,nutsuwa na zuwa ruhinta,qullin bacin ran dake danqare can wani kebantaccen saqo na zuciyarta yana neman hanyar fara kwaranyewa. Fuskokin benazeer da batoul suka gilma mata cikin idanunta,saita bude idanun da hanzari tana kiran sunan Allah. Daidai sanda suka kammala addu'an kowa ya soma miqewa domin kaiwa ga kitchen cin abincin rana.
Kaman dai da safe,komai da kowa kan tsari,sunyi lunch da lafiyayyar jallope din taliya da kuma soyayyen kifi. Wannan karon tadan cakula ta barshi kaman dai da safen,duk kuwa da cewa girki ne me kyau da bashi da makusa kwata kwata.
Sanda ta iske layin shiga wanka saita koma da baya kawai ta zauna,ta lumshe idanunta wani abu me kama da bacin rai nason sauko mata. Bakayi wanka ba tun safe,ka debo zafi da rana kazo da zummar ka wankesu kuma ka samu wannan layin da batasan ranar da zai ragu ba?.
Tana nan zaune bisa layi tana duba qaramin agogo dake hannunta,mintuna goma kacal suka rage lokacin yin wanka ya cika,a yadda kuma ameena aleeyu ta gaya mata indai hakan ta kasance kuma wanka saidai da dare,lokacin baccin rana ne. Abinda ya matuqar daure mata kai da ta gaya mata koda bakajin baccin dole nefa ka qirqiroshi
“Qangin bauta” hausar tazo mata a tsakiyar kai. Anya ama tayi mata dai dai kuwa?,wannan rayuwar da ama ta zabar mata tazo tayi da sunan makaranta irin rayuwar data dace da ita ne?,zata iya ci gaba kuwa?.
Dukkan tsammaninta ya yanke ganin mintuna biyar kacal sukayi saura,koda ta samu shiga a sannan tasan zaiyi wuya ta samu abinda takeso,tunda a qalla wankanta yakan dauki mintuna goma sha biyar kafin ta kammalashi
“Sultana mohmoud mayak’i” taji muryar Metrom asabe na kiranta. Waiwayawa tayi da fararen idanunta da suka fara laushi tana duban Metron asabe. Hannu ta sanya ta yafitota,dan jim tayi sannan ta fara takawa tana nufarta.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA*
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 33
“muje kiyi wankan kafin lokaci ya qure” Metron asabe ta fadi tana amsar mata bucket. Ba musu ta miqa mata,Metrom tayi gaba sultana na biye da ita. Duk sai su fatima suka bita da kallo,can qasan ranta itama sultanan tana mamakin yadda metrom din ta kebeta ita daya.
Toilet dinsu da iya su yasu ta sanya muqulli ta bude ma sultanan ta shiga. Duk da a tsaftace yake amma sai ta dinga jin wani bawai. Sam baiyi koda rabin toilet din da ma'aikatan gidansu ma ke shiga ba. Hakanan tayi wankan a gaggauce saboda jaddada mata iya sauran lokacin da ya rage da Metron tayi.
Koda ta isa hostel an fara counting an kusa kaiwa qarshe,hakanan tabi lafiyar gadonta ta kwanta. Bata wani matsawa kanta can bama baccin ya dauketa kasancewar tana da buqatar yinsa,don tsahon rayuwarta bata taba daukan lokaci haka yini guda tana a tsaye ba,bata jurewa wahala aam,shi yasa take gudun islamiyya kamar me?. Babban abinda ya sanya ta tsani boko kuwa baccin safe da take hana mata,ta tsani tana bacci a yanke mata shi,yanzun zakaga bacin ranta.
Ilai kuwa tana tsaka da baccin sautin muryar fatima ta ratsa kunnenta. Bata gama wartsakewa daga bayanin fatiman ba taji wannan kakkaifar muryar wadda tamkar an halicceta ne don qididdige musu mintuna ta fara musu lissafi. A kasalance ta jawo hijab dinta na house wear ta zura,ta sauke qafafunta qasa tana saukowa daga saman gadon tana jan wani mugun malalacin tsaki. Kanta gaba daya sara mata yakeyi,wannan wanne irin stress ne haka?.
Sallah suka sake wucewa sukayi cikin jam'i kamar dai ta azahar,sukayi dukkan azkar sannan suka wuce babban filin da suke zama don maimaicen karatun da akayi a ranar. Yana daya daga cikin dokoki da qa'idan makarantar. A bisa radin kansu kowanne zaiyi muraja'ar karatunsa,cikin rukuni,idan kuma anso awarwartsasu kowa shi kadai. Ajinsun ta lura suna da himmar karatu,team guda sukeyi suna yiwa juna tuni da qarin haske,a yanzun ma hannunta saman habarta,littafinta a bude amma kuma idanu ne nata. Ta baza dukkan hankali da nutsuwarta amma har yanzun bata fahimci komai ba,sai ta sauke ajiyar zuciya,wani abu yana darsuwa cikin zuciyarta,wani abu da bata taba jin irinsa ba sai a wannan karon.
Sha'awar taga ta iya karatunta kaman kowaacce daliba,tana karantashi sosai kamar yadda taga Fatima ahmad da ameena aleeyu nayi,bisa dukkan alamu ma sune jagororin zaman,ta fahimci suna ganewa matuqa,sai suka dinga bata sha'awa ta dinga binsu da kallo.
Karfe biyar suka koma hostel,masu wanka gyaran gado,saka net duka suna aikinsu,tana zaune tana sake nazarin kowa tare da bin kowa da kallo. Ameena aleeyu ta taba kafadarta tana kallonta
“Ki gyara gadonki sultana,kinsan komai namu yana da qayyadadden lokaci,qarfe shida zamu fita a nan,idan ka wuce haka kuma sai kayi zaman istigfari,ga punishment” ta qarasa fada tana dariya saboda tuna makarar da Fatima ahmad tayi wata rana da lokaci ya qwace mata
“Wai dama istigfari din da ake tsareka kayi shima wani azabar ne ban sani ba?,saika bude duk muryarka ka qwala da qarfi kamar wanda kake saka ran mutanen sama su tayaka lissafawa?” Maganar ke sanya ameena aleeyu dariya har yau,duk sanda kuman tayi dariyar fatiman tasan da ita take,to in sha Allah sai takai mata duka. Kamar yanzun ma dundu ta bita dashi tana sauke net dinta,ameenan ta qwace tana gocewa,sai Fatiman ta zarto gadon sultana tana cewa
“Tashi na kama miki mu gyara muyi mu fita da wuri” ta fuskanci duk irin gatan da suke taqama dashi sultanan ta damesu,ta sake tabbatar da hakan sanda sultana ta kasa tabuka komai. Batasan ta yadda zata kama zanin gadon ta zaunar dashi sosai saman katifar ba ballantana net din da bata taba bacci qasan net irinsa ba,na saman gadonta ba irin wannan bane sam sam sam,aba ne ya siyo mata shi musamman daga turkey,daga gadon har net din,shi kansa duk da kyau da tsadarsa bata fiya shiga ciki ba,don gidan kwata kwata basusan wai wani abu da ake kira sauro ba bare sauran qwari,gida ne dake bisa tsari yake samun cikakkiyar kulawa daga ma’aikata kowanne lungu da saqo na gidan
“Kaman haka a irin wannan lokacin muke gyara makwancinmu,duk lokaci irin wannan sai na tuna da talatu” fateema ta fadi tana dariya dariya
“Suna qoqari sosai,a lokacin bakasan zafin abun ba,sai yanzu da rayuwar makaranta ta gaya maka” ameena itama ta fadi tana tata dariyar. Lokaci lokaci sukan zauna suyi hirar masu aikin gidajen nasu,zuwansu makarantar ya sanya suka qara ganin kima da matsayinsu da kuma girman hidimar da suke musu.
Hannu kawai sultana ta sanya ta dafe goshinta,itama tanja ce ta fara fado mata,sau daya kuma koda wasa bata taba daga tsintsiya da sunan share dakinta ba,hatta suturarta idan ta cire tanja ke killace mata,me taci?,me zataci,dukka suna wuyan tanja,hatta panties nata washing machine ke hidimat wanke mata su,yau gata cikin rayuwar yiwa kai komai,ba kuma cikakken 'yancin lokaci,sai iya abinda aka qayyade maka.
“Ya Allah” karon farko ta furta sunan ubangiji da a lokacin zuciyarta ke ayyana mata shine zai dafa mata,ta waiwaya ta sake kallon gadon tana mamakin yadda fateeman ta gyarashi tsaf,ita dinma kamarta kenan take ada?,dole ta sanyata koya?,ta yaya ta kuma ina ita zata fara nata koyon?.
A masallacin sukayi magariba,suka sake komawa kitchen sukaci abincin dare,sukayi isha’i sukayi tilawar litattafan addini sannan suka wuce makwanci.
Kamar jiya din,yauma da farko juyi ta dinga yi,gaba daya yininta na yau take nanatawa cikin ranta. Wata irin rayuwa data banbanta da rayuwarta,ta banbanta da rayuwar data saba yi,yau gata tsundum cikin makaranta, makarantar da babu abinda ta tsana sama da ita,yau sai gashi ba jeka ka dawo bama makarantar kwana ce. A Hankali tunaninta ya gangaro kan yadda rayuwar karatunsu take. Kowa kusan gwanine za’a ce cikin daliban,tana hangen yadda kowa ke zagewa ya kuma dage don ganin ya kai maqurar iya karatunsa,ta tuna yadda a kowanne darasi ta dinga baza idanu,nan da wani lokaci idan batayi da gaske ba zata zama cikin sahun dalibai na kashin baya,wadanda kowa zai fahimci qarancin ganewarsu. Wannan tunanin ya sanyata hantsilowa daga gadonta,wani abu yana dasa mata qaimi cikin zuciyarta,tana jin ba zata lamunci faduwa ko rashin iyawa ba. Ta saka hannu gefan gadonta inda qaramar locker dinta take ta fidda jakar makarantarta,ta zazzage dukka litattafan da a yau sukayisu,ta soma budesu daya bayan daya tana dubawa.
Da qur’ani ta fara,ta dinga hada baqin yana guduwa,ta dinga qoqarin maimaita shafukan daidai,a haka ta kashe awa daya kusan da rabi kafin taji ta fara kama hanyar karatunta bisa qa’ida. Bata sare ba bata kuma gaji ba,tayita nacin maimaitawa har sai da taji ya zauna mata a harshenta,ta tabbatar zuwa gobe koda za’a ci gyaranta kadanne. Kowanne subject sai da tayi maimaicinsa,tun bata fahimtar abinda take ta faman karantawar har sai da taji kamar qwaqwalwarta tana budewa ne a hankali. Sanda ta duba agogo awa uku kacal ya rage lokacin tashinsu dsga bacci yayi. Sai ta zauna tsakiyar gadon tana son tuna addu’a daya daga cikin tarin addu’o’in da taji suna yi,yayin tashi a bacci,kwanciya bacci,cin abinci,shiga bandaki,shiga aji da komai ma na rayuwar daliban makarantar. Ba wani abu guda da taga wani dalibi yayi bs tare da yayi addu’a ba,tamkar ma ta shiga jinin jikinsu ne sun kuma saba. Duk sallolin da akayi yau din cikin jam’i abinda bata taba yi ba tsahon rayuwarta……duk sanda aka idar suka hada baki duk yawansu suna addu’o’in da akeyi bayan idar da sallah,sai taji wani sanyi dadi da nutsuwa suna shigarta,sai taji wani sukuni yana ratsata,har sai taji kamar ma kada lokaci ya cika, kamar kada su daina addu’ar.
Waiwayawa tayi ta dubi su fatima dake bacci abinsu. Cikin ranta ta ajema kanta zasu zame mata mudubi in sha Allah cikin rayuwar makarantar,zata kuma yi qoqari tayi catching up na dukkan abinda suka tsere mata.
Abunda ya bawa su fatima mamaki a yau ita ta tashesu maimakon jiya da sune suka tasheta,kafin kace meye ta kammala komai da sukeyi kafin fita masallaci sallar asuba. A bakin hostel din suka cimmata tsaye da metron asabe tana gaidata
“Ina fatan baki da wata matsala ko?,idan kun kammala karatu kina da sha’awar wanka kafin ki wuce aji kiyimin magana saiki shiga kiyi”
“Ba komai,zan jira har lokacin da kowa yakeyi,idan ban samu toilet ba zan miki magana sai nayi s gurarenku din” ta amsa mata tana rungume da qur’aninta cikin wata murya me sanyi. Da kallo metron asabe ta bita,bata taba zaton zata sameta da sauqin kai har haka ba,bata taba kawowa cewa zatayi saurin daukan shawararta ba,sai gashi daga jiya zuwa yau kacal tana qoqarin kiyaye dokar makarantar.
Yadda ta dinga nacin bibiyar kowanne harafi da ake qara musu ya sauqaqa mata qwarai. Kafin akai ga tashi sai gashi ta iya karatun fes kamar kowa. Dadi sosai ta dinga ji cikin ranta,har kuma hakan ya nuna a fuskarta,duk da ba murmushi takeyi ba amma fuskarta a washe take sarai.
Gurin sharar compound na hostel dinsu kuwa kamar kowa ta karbi tsintsiya. Metron asabe na cewa ta bari amma tace zata iya. Tana sharar tana mamakin meye dalilin metron asabe nason dauke mata wasu wahalhalu na makarantar ne?,me yasa take kawo mata hanyoyi sauqi da sauqaqawa?,ahalinta ne fa da hannunsu suka danqata a makarantar,komai na ama bisa manufa da tsari yake,ta tabbatar ba a banza ama ta aikata hakan ba,ba shakka akwai dalili,kuma akwai hujja.
Koma meye ita dai ta barma ranta zata rayu kamar kowa,tayi alwashin zatayi irin rayuwar data samu cikin makarantar,zata rungumi kalar sabuwar K’ADDARAR da ta risketa. Can kuma qasan ranta takejin kamar dai ama ta kawota ne don tasan rayuwa?,kamar dai ama ta kawota ne don ta fahimci bayan duniyar da take rayuwa a ciki akwai wata duniyar ta daban?,kamar dai ta kawota ne saboda wasu abubuwa masu yawan da ita kanta bata gama fahimtarsu ba.
Tana ankare da yadda labour prefect huda keta wani fusge fusge da sanya mutane aiki cikin izza da gadara. Duk wanda ta kira ita da team dinta da sassarfa yake isowa ya kuma zube yana kiran
“Aunty gani” ladabi ne wannan na makarantar da dole kowanne dalibi ya koya ya kuma ginu akai,amma batajin zata iya zube musu har haka,hasalima batajin tana da LOKACIN shiga sharafinsu.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 34
Lokacin data sake kame kanta tare da takatsantsan da lamarin huda da sauran maqarrabanta ita kanta sai tayi mamakin kanta,har batasan sanda qaramin murmushi ya subuce mata ba abinda ta jima bata yishi ba,wai yau ita sultana ita ke kaucewa rigima da wasu,ita sultana da batajin tsoron rigima da ko waye,mace ko namiji,yaro ko babba,bata tsoron tunkararka ko qaddamar maka,lallai giwa tayi lafiya ta fadi qasan zuciyarta tana shafar gefan fuskarta,to ko hankali ta soma yi?,ta yiwa kanta tambayar data sanyata sakin wani murmushin.
***A hankali A hankali cikin wani irin yanayi sauyi na bazata ke ruskar rayuwarta. Ingatacce kuma gamsashen sauyin da yayi nasarar taba ainihin ruhi da zuciyarta. Cikin ba zatar da ita kanta bata sani ba ta tashi daga SULTANAn bibi,sultanan aba sultana ta nijer zuwa sultanan Nijeria,sultanan hassan Ibrahim gwarzo,sultanan fateema Ahmad da kuma ameena aleeyu. Ba wanda take bari ya huta tsakanin fateema Ahmad da ameena,kowannensu ta samu ta riqeshi to tabbas sai yayi mata qarin dukkan wani kwantan karatu da aka tsere mata,tashin cikin dare ya fara bin jikinta,a lokacin da kowa ya sanya haqarqarinsa yake bacci…..a lokacin take tashi bita da tilawar katatuttukanta. Cikin kowanne mataki na karatunta batajin akwai ya kamar ALQUR’ANI. Tana jinta wani fresh a sanda take karantasa,tana jin wani softness cikin zuciyarta,tana jin kuma nutsuwa tana shigarta,shi ya sanya cikin lokaci qanqani ta kamosu ta kuma hade da izifin baya da suka wurwuceta,abinda ya baiwa kowa mamaki,sauri da kaifin basirarta,duk da a farko sun mata kallon hadarin kaji,kallon dalibar da bazata wani basu matsala ba. Tana da rivals da yawa a ajin,matan da sukaci buri suke ganin sune na gaba gaba wajen samun yarda da amincin malamansu,sai gashi cikin dare daya wata baquwar haure na shirin yi musu shalll. Wata irin murya Allah ya mallaka mata me dadi,sai take sake qawatuwa da sautin karatun qur’ani da wani irin daddadan sauti.
Bata da lokacin kowa,ba wanda take bi ta kansa,bata kuma hulda da kowa idan ka debe fateema da ameena. Muddin kaga hirarta sosai to da sune,idan kaga motsawa kumatu da labbanta to da ameena dinne,sun dinke sun zama kaman wasu 'yan uwa, dabi'a da yanayin sultana din su ke burgesu,suna mata kallon wadda gayu gata da shagwaba suka yiwa yawa shi yasa komai nata ya fita na dabanne.
Kowanne kwanan duniya sai metron asabe ta tambayeta ko tana da wani buqatar?,amsarta daya ce A'ah,a nata tunanin tanason gwadawa ama zata iya rayuwar data zabar mata,zata kuma wanzuwa a kowanne bigire ko muhalli da rayuwa ta gangarata cikinsa.
VISITING DAY
Tun daren jiya daukacin daliban makarantar ke cikin farinciki da walwalar ganin ahalinsu a goben,kamar yadda fateema da ameena aleeyu suka bi sahun sauran dalibai.
Safiyar yau din kowa shiryawa yakeyi don 'yan gidansu su ganshi fes..... sultana na zaune kusan sai da kowa yayi nisa wajen nashi shirin,wasuma suka soma fita sannan ta shiga tayi nata wankan da yau ta zabi tayi cikin tsaftatattun toilets dinsu ba nasu metron asabe yadda ta saba yi ba.
Komai nata cikin wani sanyi da nutsuwa ya koma,babu sultanan nan ta anihi,haka ta tsaya gaban gadonta ta shirya kanta cikin house wear kaman kowa,bayan ta daure jelar manyan kitson da fateema da ameena sukayi taron dangi sukayi mata,saboda sulbinsa da tsahonsa ya sanya ba kasafai take kitso ba,koda anyim ma baya dogon zango yake warwarewa.
Tayi kyau sosai,don sabbin house wear ta sanka,dinkin kuma ya zauna sosai ya qara fidda tsaho data qara,saidai kuma tadan fada kadan wanda hakan baya rasa nasaba da sabuwar rayuwar da take qoqarin daidaita kanta taga ta hauta bisa tsari.
“Sultana mohmoud mayak’i” aka maimaita kiran sunanta har sau uku. Waiwayawa tayi tana duban me kiran nata,senior dinta ce cikin wadanda zasu fita makarantar a shekarar da ake ciki
“Kina da baqo” ta fadima sultana din tana juyawa. Turarenta ta miqa hannu da sauri ta dauka ta fesa ta maidashi,sannan ta zura house shoe dinta ta soma tattakawa cikin wani irin zumudi tana ratsa hostel din nasu
“Tacan zaki zagaya” dalibar ta fadi tana mata nuni da hannu sannan ta wuce gararin gabanta.
Sosai take takawa da zumudinta shiyyar da ta nuna matan,qasan ranta cike fal da dokin ganin ama da aba,tasan kuma zaiyi wuya ace bibi batazo mata ba,BATOUL da BENAZEER......taji an kira mata sunan yaran daga can qasan zuciyarta,ta lumshe idanunta murmushi na subuce mata,wata irin mahaukaciyar kewar yaran ta taso ta lullubeta,karon farko daga can qasan ranta taji wani irin tausayinsu ya saukar mata.
Tsaiwa tayi cak ganin tana ta cusa kai area din da babu motsin kowa babu kai kawon kowa. Ta tayi ta tsaya cak,wai mema dalibar tace mata ne
“Kinyi baqo” ta tuna da abinda tace
“Baqo……baqi….” Sai taji kwanyarta ta rikice. To ko aba ne shi daya ya samu zuwa?,idan hakane ai ba za’a barshi ya qaraso har gate na biyu na sashen mata ba,akwai askar da basa bari maza su wuce gurin,kuma bata nan ya kamata ya tsaya ganin nata ba.
Wani mummunar bugawa zuciyarta tayi. Cikin jini tsoka da jikinta taji kamar ana fusgar hankali da kuma numfashinta sakamakon shaqar wannan qamshin…….wannan qamshin dai da hanci zuw qwaqwalwa ba zasu iya gaza fayyaceshi ba,wannan qamshin dai da yake da taushi dadi da laushi……amma a nata hancin kama yakeyi mata da qamshin MUTUWA…..Tabbas inda mutuwa tana da wani qamshi na daban……wannan qamshin shi ya dace a baiwa wannan sunan.
Waige waige ta fara yi jikinta yanason fara rawa, hankalinta kuma nason yin qaura daga gangar jikinta
“Ki nutsu,ba kowa a wajen nan,ba shi daya aka qerowa turaren ba,bashi daya kaf duniya yake siyan turaren ba……ki nutsu kada ki ruda kanki sultana” zuciyarta ta fara rada mata cikin kunnuwanta yayin da qirjinta ke wani irin bugawa da tsananin qarfi har numfashinta yana rarrabewa.
“Sultana mohmoud mayak’i” ta sake ji an kirata,kiran sunan da ya hautsinata gaba daya ta waiwayo da wani irin sauri. Wata dalibar ce cikin daliban da suke ajin farko wato J.s one ke nufota. Hannunta riqe da wani babban abu da ya yima sultana zubi da kwali. Har ta iso gabanta sultana na dubanta qirjinta kuma bai fasa dagawa ba,sai ta miqa mata kwalin tana kallonta bayan ta rusunawa sultana din kamar yadda yake doka ne na makarantar dole na qasa ya rusunawa babba
“Wai gashi” bin kwalin dake hannun yarinyar tayi da kallo sannan ta maida dubanta ga fuskarta tana tattaro ragowar miyau din bakinta,da qyar ta tambayeta
“Wai inji wa?” Kai ta karkada yarinyar
“Ban sani ba,nima wata daliba ce ta bani tace itama wata ce ta bata tace a baki” fuska tadan motsa kadan,abun yadan daure mata kai,tayi kaman ba zata karba ba,to amma yadda yarinyar ke rusune sai taga bai kamata ta barta a haka ba
“Ya sunan wadda ko wanda ya bada?”
“Nima na tambaya tace bata sani ba,wancan din tace me bada saqon sunanki kawai ya kama yace a baki”
“Kodai aba ne yake sauri bazai iya tsaiwa ba ya bayar a kawo?” Wannan tunanin ya sanyata miqa hannu ta karba,yarinyar ta juya da sauri sauri tana barin gurin don kada azo mata ba’a sameta ba,sai itama sultana din ta soma takawa tana riqe da kwalin tana barin wajen zuwa nana aisha hostel,har a sannan hancinta yana jin qamshin nan data yiwa maqurar tsana.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 35
Tana tafe a hanya tana juya kwalin,ba qato bane hakanan ba qarami ba,yana da matsakaicin girma,amma kuma yana da dan nauyi. Kai tsaye ta koma hostel dinsu,sanda ta isa dakin da yawa an yoye,kowa ya fita waje,wasu gurin family dinsu,wasu kuma suna jiran tsammanin isowar 'yan uwan nasu.
Gefan gadonta ta zauna a nutse,ta aza kwalin saman cinyarta ta fara budeshi.
Sannu a hankali ta kammala yage takardar jiki tsaf,wani irin kwali ne na musamman tamkar qaramin akwati,sai daukan idanu yakeyi da wani irin santsi da tambarin dolce and Gabbana ko ina a manne a jiki.
Doki ya kamata,muddin wannan kyautar daga hannun aba take to ko shakka batayi tafiya yayi ya kuma tuna da ita
“Allah sarki ubana,maganin kukana” ta furta hawayen qaunar aba na cika mata idanu.
Cak ta tsaya tana duban kyaututtukan da aka shirya cikin box din. Tarin tsagwaron chocolates,dukka kalolin wasu chocolate da takesha babu wadda ba'a zuba ba a cikinta. Wani siririn agogo da take da tabbacin zaiyi wuya chain dinsa idan ba gold bane a jiki. Turaren da take amfani dashi sanda tana sultana dinta wanda a yanzun ma tuni ta sauya zuwa wani kalar daban. Biro da wasu qananun notebook masu masifar kyau da tsari,sai wata memo itama daban da zata baka damar tsara komai na rayuwarka da date da komai,sai wani greeting card da duka rubutun jiki layi qwaya daya ne tal
“Best wishes” kadai ke rubuce daga tsakiyansa.
Bin budadden box din kawai takeyi da kallo,cikin jikinta ta dinga jin wannan kyautar ba daga hannun aba ta fito ba,batama dace da ace daga aba din take ba,to anya ba batan suna sukayi ba?,tunda dai daliban makarantar ba suna da yawa qwarai,kuma bazaiyiwu kaf makarantar ace ita daya ce qwallin qwal me suna sultana mahmoud ba. Juya bayan katin tayi,a nan ta samu amsar tambayarta,cikakken sunanta harda na qasarta ne rattabe a bayan,hakan yana nufin me aiken yanason bata tabbacin saqonshi ne.
Wani abu me kama da bacin rai ya biyo bayan mamakinta,ta sake juya katin ko zataga alama koda ta sunan me saqonne amma babu,tsoro da shakka suka kamata,daidai sanda ameena aleeyu ta shigo da sassarfa
“To kizo ga duka ‘yan gidanku nan gaba daya,har mun gaisa da aba ma,ama nada maqurar kirki,atta da almu suna yanayi dake” ameena din tace da sultana cikin nuna zallar zumudi.
Da sauri ta tashi hae box din dake saman cinyarta ya watse a wajen,sam batabi ta kansa ba tayi hanyar waje duk da tana jiyo ameena na fadin
“Kinyi barna,wannan agogon me tsada …….Allah yasa baki fasa glass dinshi ba”.
Tana tafiya zuciyarta na nanata tambayarta daga ina wannan gift din ya fito?,indai har ga aba yazo to waye ko wace ta aiko da gift din?.
“May be dai still aba dinne” zuciyar dake neman nutsuwarta ta fada tana bata tabbaci.
Tun daga nesa data hangosu murmushi ya subucewa fuskarta,kasa jurewa tayi ta isa garesu a hankali sai ta dan saka da sassarfa,ta qarasa ga ama ya fada jikinta tana riqeta da kyau,bakinta har rawa yakeyi wajen fadin sunanta
“Ama…..sannu da zuwa ama”
“Wato ama dinki kawai kika gani ko?,ni baki ganni ba?” Muryar bibi ta doki kunnenta. Waiwayawa tayi da sauri tana duban bibin,sai ta saki ama ta nufeta itama ta fada jikinta tana qanqameta
“Ban lura da bibi na ba,bibi tun daga nijer kikazo ganina?” Ta fadi tana murmushi. Harara ta balla mata
“Kuma gashi an yanqwanani ko ganina ma ba’a yi ba?” Ta fadi tana yatsina baki,saidai kuma qasan zuciyarta na mata wani irin sanyi saboda sauyi muraran da take gani tattare da sultanarta. Baya taja tana duban bibin
“Ni ya kamata nayi fushi bibi,kina can kina qiba abunki aba yana baki kayan dadi,ina nan kin barni da abinci da horon boarding” ta dan taba tsokanarta wanda abune da kusan dukkaninsu kunnuwansu sun manta rabon da su jishi daga bakinta,sai suka sanya dariya,wanda muryar aba ta fito a ciki,sai a sannan ta ankara dashi shima,abinda ya sanya tadan yi qas da kanta ta kuma nufeshi da hanzari.
Zamewa tayi ta tsugunna a qasa tana gaidashi
“Barka da warhaka aba,ina kwana?” Ba wanda bai dubeta ba yadda take komai cikin nutsuwa da tsantsar girmamawa. Yana dan saki murmushi ya amsa mata
“Lafiya qalau sultana,tashi a qasa kada ki bata uniform dinki,ga abun zama can an shimfida mu qarasa” tanja ce ta riqe hannunta,saita waiwaya tana duban tanja din
“Kina Nigeria ko kina nijer tanja?” Ta tambayeta bayan ta gaida tanjan itama cikin rusunawa,abinda sultana din bata taba mata shi ba koda wasa,kai kwata kwata ma ba zatace ga sanda sultanar ta taba gaidata ba,ba zata iya tunawa ba.
“Inaaa……ina nan gurin iyayen dakina,in tafi nabar ‘yan biyu?,ai bazan iya ba” ta amsa mata tana murmushi. Sai a sannan hankalinta yakai kai,bataga benazeer da batoul ba,idanu ta shiga warewa can qasan zuciyarta tana jin shauqin ganin yaran,amma ko me kama dasu bata gani ba. Duka sai taji zuciyarta ba dadi,ta dinga nacin kallon inda goumar yake amma bataga alamun suna tare ba,har goumar din ya lura da yawan kallon da takeyi,sai ya saki murmushi ya watsa mata hannuwansa,qasa qasa kuma yadda babu wanda zaiji yace da ita
“Me na satar miki ne kuma yau?,mutumin da ko kallon fuskarsa ba’a sonyi yau shi aketa kalla?,ki bude baki kawai ki cewa ama ina ‘ya’yanki ko?” Harara ta watsa masa gabanta yana faduwa,salon maganarsa sak yaa maina,kusan wasu abubuwan nasu suna bala’in kamanceceniya da juna,kamannin fuska ne sam Allah bai sanya sunyo daya ba. Qaramin tsaki taja tana dauke kanta ta maida ga sashen su ama daketa bata labarin abubuwan da suke wakana bayan batanan,sai muryar goumar ta motsa cikin dariya
“Allah bibi wannan ‘yar jikanyar taki ladabin qarya tayi muku,qanzo ne ya sanyata yin laushi,bata canza hali ba ashe rashin kunyar nan tana nan,yanzun nan ta gama min tsaki harda harara” ya qarasa fadi yana dariya sosai. Harara bibi ta watsa masa
“Qaniyarka sarkin sharri,ta ina ta hararekan dukkanmu muna nan idanunmu suna gani?”
“Wannan idon naki ai ya kusa rubewa,don inda kina gani sosai da a yanxun kinga wani abu da ni kadai nake hangowa” ya furta maganar yana kallon wani guri daban. Ba tare da Bibi din ta waiwayo ba tace
“Kaji dashi ja’iri” saita jawo wani mazubi ta miqawa sultana,wanda ba komai ciki sai kayan ciye ciye da tasan tafiso.
Cikin wata irin sassanyan nutsuwa ya maida wayar tashi me bango biyu ya manneta guri guda ya rufeta. Qirjinsa da zuciyarsa tana masa wani irin nauyi,da gaske goumar yakeyi bazai taba ganin yaran ba?,da gaske yake,yau din rana ce da zata iya sake nesantashi da damar sake ganin kowa da komai da ya shefeshi ko ahalinsa.
Yayi kwadayi qwarai wajen sakasu a idanunsa,yaso ya samu wannan damar koda zata kasance dama ta qarshe a garesa,tunda bai san yaushe ba?,baisan sai wanne lokaci ba.
Wannan babbar dama ce a gareshi da muddin ta gushe masa baisan sai yaushe zai sake samun wata damar makamanciyarta ba,zaiyi komai zaije zai kuma aiwatar dukka domin sa,domin ahalinsa.
A hankali ya isa dab da motar da mutumin da idan baka matso kusa dashi qwarai ba zaka tsammaci mutum mutumi ne. Yana isowar ya sanya hannu ya bude masa bayan motar,ya zura gangar jikinsa cikin wata irin kasala da galabaita tamkar wanda yayi watanni yana aikin kauda duwatsu ba tare da ya huta ba. Wata wawiyar ajiyar zuciya ta subuce masa,ya lumshe kyawawan idanunsa yana jin kamar ajiyar zuciyar zata fita ne tare da zuciyar dake qirjinsa,ya maida bayansa jikin kujerar yayi relax yana jin yadda zuciyarsa ke tsananta bugawa sanda motar ke gangarawa tana barin wajen.
Har ta rako su aba bakin mota,suka kuma fidda komai da komai da suka kawo mata cikin zuciyarta bata kasa juya batun box dinnan ba,daga ina yake?, itace tambayar da taketa nacin nanatawa.
Tana nan tsaye har suka kammala shiga motar. Ama ya sauke glass din bangarenta ta miqa ma sultana wani box. Kallonsa tayi sannan ta sanya hannu ta amsa. Madararta ce,madara mafi soyuwa a gareta,madarar da tana begenta amma kuma tana nisantata da rayuwarta saboda tuna mata da takeyi dashi
“Gashi inji benazeer da batoul da baki tambayesu ba,sunce suna gaidaki” wata irin kunya ce ta saukar mata,tanason tambayarsun amma batasan ta yaya zata fara tambayar tasu a gaban ama da aba din ba,uwa uba ga bibi a gefe,ga kuma dan sanya ido goumar
“Ace ina gaidasu” ta fada da sassanyan muryarta
“Basa amsawa,sai da aka roqa musu” goumar ya fadi cikin salon tsokana. Harara kawai ta samu damar binsa dashi saboda tashin da motar tayi bata samu daman maida masa raddi ba.
Duk wata kujiba kujiban zuwan masu visiting lokaci yana yi aka rufe gate din makaranta,doka kuma taci gaba da aiki. Suna saman gadonsu kowa na kintsa wajensa da gyara kayayyakin da aka kawo masa daga gida,dakin nasu fal kaya saboda dukkansu kusan daga gidan iko da wadata kowacce ta fito,babu wadda ta fito daga qaramin family.
Da wuri sultana ta gama komai,tana daga saman gadonta ameena aleeyu ta qaraso da box dinta ta miqa mata
“Ga box dinki nan” binsa tayi da kallo tana jin shakkar amsa,sai ta maida dubanta ga ameena
“Bansan waye ya aiko dashi ba,ki ajjiyemin kawai zan nema maishi saina karba”
“To ya wuce saurayinki?” Ta tsokaneta tana dariya. Dukanta maganar tayi har tsakiyar zuciyarta,sai ta daga kai tana kallonta gami da jefa mata harara
“Ba saurayi ba dattijo” ta fadi cikin hushi. Yanayin yadda tayi maganar gauraye da harshen qasar nijer cikin kuma fushi dukkansu ya basu dariya,bata sake ce musu komai ba ta janye qafafunta zuwa gadonta ta juya musu baya.
Iyakar tunaninta kaf ta gaza canko wanda zai iya aiko mata da saqon
“To kodai goumar ke yimin wasa da hankali?” Tayi tunanin haka daga qarshe,sai ta cije lebanta tana jin qamshin gaskiyar hasashenta. Tabbas da ta tuna hakan kafin su tafi saita yayyaba masa magana,ta fuskanci kamar yana yawan son yiwa rayuwarta shishshigi.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 36
****Sannu a hankali rayuwa taci gaba da tafiyar mata,tana sake hankali tana kuma sake fahimtar me ainihin rayuwa ke nufi kadan kadan.
Sosai kwanyarta take budewa,a hankali kuma ta fahimci gatan da ama tayi mata data kawota makarantar. Kafin takai ga zuwa ss3 ta zama wata sultana ta daban. Azkar ya kama bakinta ainun,karatun qur'ani da wata nutsuwa dake nuna sanin haqiqanin rayuwa. Tabbas! Ilimi wani irin haske ne da babu irinsa,wani abu ne dake busawa zuciya da rayuwa wani ruhi na musamman. Hatta da kamanninta sun sauya,sun cika da wata irin nutsuwa da wani sirtaccen kyau nata dake boye. Idan ka kalleta a sannan babu abinda zakaji cikin zuciyarka dangane da ita sai tsananin burgewa,saboda wata kamala annuri da kwarjini da ilimi ya zuba mata,komai nata sai ya zama cikin nutsuwa da kuma kamun kai. Kalaman bakinta sun canza sosai,hakanan mu'amalarta,saidai kuma tun wancan sanyin da tayi.....tun wancan sauyawar......tun a wancan lokacin har zuwa yanzu sai ta zama me matuqar sanyi,miskila mara yawan surutu hayaniya ko kuma kwarafniya kwata kwata.
Tana S.S3 ama ta saka su benazeer a free nursery,surutu da wayonsu ya isa,wani irin wayo ne dasu da yafi na shekarunsu,duk da batoul nada kalar nata miskilancin,amma tun kafin shekarunsu su fara nisa kamanceceniyar halayya wajen yawan surutu rigima da rawar kai na sultanan can baya benazeer ta kwafe tsaf!,wannan ya sanya ama tafi maida hankali akan benazeer din sosai,tanaso dukka wadannan halaye da Tayo gadonsu su kasance kan tsari da kuma cikakkiyar kulawar tarbiyya. Saboda kwadayin ingantar tarbiyyar yaran ya sanya gaba daya ama ta daina tunanin komawa nijer,tafison a nan din inda suke suyi tasu quruciyar da wayon,saboda itace babbar shaidar banbancin tarbiyyar da qasashen biyu ke dashi.
A shekararta ta qarshe a makaranta ta yiwa kanta gata me tarin yawa. Tayi joining classes da akeyi na musamman bayan wadanda suka zama wajibi. Litattafai ake musu na addini masu yawa,zazzafan karatu ne da ya sanya da yawa daliban basu fiya joining ba sai masu wayo da masifar nacin so karatu irin sultana. Yadda zazzafar qiyayyar karatu ta juye mata zuwa zazzafar soyayyar karatu tana bawa ama mamaki. A duk sanda sukayi hutu tazo gida yakan zamana kamar ba hutu ta samu ba. Duk bayan kowacce daqiqa tana maqale da litattafai,wani lokaci hadda takeyi wasu lokuta kuma tilawa. Ta samu hadisai sosai,wasu ta haddacesu ne,musamman wadanda keda alaqa da mu'amala da kuma rayuwa,wasu kuma a yayin da aka karanta mata ta iyasu a rubuce kuma tana tsintar wasu tana amfana dasu. Kosu benazeer bata basu lokacinta kamar yadda take bawa litattafanta. Sai ya zamana ba wata shaquwa bace can can a tsakaninsu da ita. Da ama suka budi idanu,ama itace mommansu,ita sultana AUNTY kawai suke kiranta,kuma suna mata kallon auty dinsu ce,saboda tsakaninsu hukuntawa ne da tsawatarwa idan za'a yi ba dai dai ba tamkar na qaramin yaro da babbar yayarsa.
Watannin qarshe da suka rage musu a makarantar,dab da zasu fara jarabawa sukayi saukar alqur'ani me girma. Kyawawan qira'o'i dukka guda bakwai din da muke dasu babu wanda bata iya ba. Karatu take tartilan babu gargada,babu bata,zakayi tsammanin ta jima da saukeshin a yanzun maimaici kawai takeyi. Tana cikin zaqaquran dalibai guda goma na farko da aka fidda cikin ajinsu.
Sanda suka fara jarrabawa dukka tunaninta sai ya sake fadada akan qara nisan zangon karatunta,batajin zata zauna haka,yanzunne ta soma jin gardin ilimi,ashe ilimi dadi ne dashi har haka?,ashe muddin kana da ilimi kuma kana aiki dashi basai an zauna ana fama wajen gyaraka da saitaka ba?. Sau tari idan su ameena aleeyu sukaga tana zaune guri daya tana murmushi sukan cika da mamakin meye yake sata nishadi yayin kadaicewa ita daya?. Murmushin ta kan fita ne a duk sanda ta tuna da quruciyarta,ta tuna da rayuwarta a niamy,ta tuna irin tabara da rashin hankali da zallar wauta data tafka,yadda ta qaunaci rawa,xuwa party zuwa birthday kamar hauka,a yanzun idan dukka ta tuna wannan sai kunya ta kamata. Ta sake tabbatarwa da lallai komai lokaci gareshi,komai kuma yana zuwa ya shude ne cikin rayuwa tamkar a allon majigi.
Abu guda daya ke zuwa ya tsinke kyakkyawan zaren wannan tuna baya nata,idan ta tuna da MAINA. Komai yana shafewa a zuciya da ruhinta,komai yana shafewa daga tunaninta amma banda abu daya,banda MAINA banda yadda ya yiwa rayuwarta da mutuncinta dirar mikiya,banda yadda ya wargaza mata kyakkyawar rayuwa yabar mata wata rubutacciyar qaddara a rayuwarta,ya kuma shura qafafunsa ya bace battt daga sararin duniya tamkar zuwan walqiya da daukewarta. Komai ya sauya cikin rayuwarta amma wannan tabon yana nan a zane radam......wannan tsumammiyar qiyayyar tana nan a rubuce dara dara bata kauce ba,daga qarshe takan buge da xubda hawaye me tarin yawa.
Takan jaye jikinta daga cikinsu fateema Ahmad duk lokuttan da suke hirar samarinsu,soyayya ko hirar data shafi 'yammatanci,saboda a sannan kowacce ta soma cika mace,takai kuma ganiyar 'yammatancinta. Cikin jiki da ruhinta takejin kwata kwata bata cikin sahunsu,to meye zai zaunar da ita a cikinsu ana hirar da ba layinta ba?.
Su kuma dukkan wannan sun azashi ne cikin zallar miskilanci irin na sultana,son zaman kadaici da zaman shuru,kamewa da rashin son hayaniya. Takan saki siririn murmushi da jerarrun fararen haqoranta a duk sanda suke mata tsiya
“Kin fiya shuru shuru wallahi,ke ba dama ki zauna ayi hirar arziqi dake.”
“Baku riski sultana a sanda take sultanan ta ba,kun samu sultanar nijeria ne,sultanar hassan Ibrahim gwarzo,sultanan ama,auntyn benazeer da batoul…….ba sultanan nijer ba,sultanan bibi da aba,da hirar tsiya ma duka sai anyi,saikun nema wajen fakewa daga gareta” takan raya haka ne cikin zuciyarta.
Ta riqi sallah sosai,ta kuma koyi azumin litinin da alhamis a gida ko a makaranta,tun daga sanda suka karanta hadisin dake bayanin falalar azumin litinin ko alhamis basu taba ruskarta tana da cikakkiyar lafiya ba tare da tayi azumin nan ba. Saidai har yanzu jikin nan yana nan ba wata qiba,amma kai tsaye ba zakace a rame take ba,sai tsaho data qara,duk wata halitta tata ta qara cika,kyawun nan na cikakkiyar buzuwar asali,jinin NADEEYA MUHAMMAD MAYAK'I ya hudata sosai,ya zamana har hirarta akeyi sashi sashi cikin makarantar,domin kaf cikar makarantar da batsewarta babu wata diya mace data isa ta tsaya a tudun mizanin kyau tare da ita,wannan ya sanya take sake kame kanta da kuma fita a dukkan shirgin da ba nata ba. Sai kuma Allah ya zuba mata farinjini da kwarjini wajen juniors,bata da mugunta ko kadan,hasalima cikin sabbin shigowar nan duk yarinyar da ta gani ne rawar kai iyayi da surutu sai taji tana tausaya mata,wani lokaci kuma ta saki murmushi don suna tuna mata da shekarun baya da suka shude mata.
GRADUATION DAY
Rana ce me matuqar tarihi cikin rayuwarta,ranar data sanyata xubda hawaye me yawa,ranar data sakata dana sanin zaman da tayi ba karatu a wadancan shekarun,ranar kuma data sakata a godiyar Allah me tarin yawa daya fiddata daga duhu zuwa haske.
Taro ne akayi gagarumi na saukar dalibai tare da yayesu,tana cikin dalibar farko da aka kira aka karramata har hawa uku gaban dubban al'umma,gaban familynta,gaban mutanen da suke tamkar iyaye a wajenta,gaban mutanen da suka debe tsammanin zamantowarta a yadda take a yanzun.
Duk inda ta motsa kyaututtuka ne na yabawa da karramawa. Da yawa mutanen dake wajen da sukasan family din MAYAK'I sun mata kyaututtuka na alfarma,har sai da goumar ya taso ya dinga tayata karba.
Data dawo mazauninta ta zauna kasa jurewa tayi,taja hijab dinta ciki ta boye fuskarta tana kuka. Abun mamakin sai batoul ta kalli benazeer cikin kwabe fuska kaman zata saki kuka
“Benz(haka take kiranta don bata iya kiran full name din ya mata tsaho da nauyi),waye yasa aunty kuka?” Waiwayowa benazeer din tayi ta zubawa sultana idanu,itama sai ta kebe baki kamar zata sanya kukan tana duban goumar
“Oncle…….ko itama aunty ta tuna da daddynmu da kace yayi tafiya?” Sosai maganar ta doki qirjin sultana,har batasan sanda ta fidda rabin fuskarta ba tana duban goumar. Kamar dama ya shiryawa hakan,shima ita yake kalla,suka zubawa juna idanu na wasu lokutta suna kallon kallo. Tanata hadiye bacin ranta da maganganun da takeson gaggaya masa saboda cikin bainar jama’a suke. Wato kebewar da yake da yaranta har gaya musu yakeyi suna da wani daddy da yayi tafiya?,waye ya sashi?,shi awa?,meye hadinsu da daddyn da yake musu maganarsa?, tabbas ba zata qyaleshi ba,sai tayi warning nasa,kada ya sake bari wannan maganar ta shiga kwanyar yaranta,bata buqatar hakan.
Wannan maganar kawai ta dauke hawayen fuskarta,sai suya da zuciyarta keyi mata tana fakon goumar tana jira su samu matsawa daga wajen ta amayar masa da abinda ke cikin ranta.
Bata samu wannan damar ba sai da suka tashi komawa gida,bayan taro ya watse,makaranta ta sallamesu sai kuma zuwa karbar result na exam dinsu. Ta gama koke koken rabuwa ita dasu fateema Ahmad da ameena aleeyu,aminan qwarai da ba zata taba mancewa dasu ba,sunyi exchanging phone numbers da full address nasu,har Adress dinta na nijer dukka ta basu saboda batasan me rayuwa ta tanadarwa gobenta ba, al’amuranta bata fiya basu amana ba,ta fahimci caccanjawa sukeyi a duk sanda sukazo hakan,koda yake umarni ne daga rabbussamawati.
Ita da aminata,najma da yasmine su ya dauka a motarsa wadda bai jima da siyenta ba bayan kama aikinsa baya bayan nan da kammala karatunsa. Kusan duk wani hali da dabi’a na maina yana dasu. Har rabon motoci aba ya yiwa samarin cikin dangi yace bazai amsa ba,yafison ya fara hawa wadda ya siya da guminsa. Kusan aqidar maina ne,neman nakai,ya tsani a masa alfarma,ya tsani ya rabu da wani ya dinga cin albarkacinsa,wannan dalili ya sanya har yabar gida baida motan hawa na kanshi,duk da cewa akai akai yana bisa hanya duk kusan sati ko sati bibbiyu tsakanin niamy da marad’i.
Ta fahimci akwai wata kyakkyawar alaqa tsakaninsa da najma,saidai a yanzun ba komai take magana akai ba shi yasa batace komai ba,amma tunda su aminata sukazo ta karanci akwai gulma fal bakinsu,bata dai tsaya ta basu lokaci bane,amma ta tabbatar sai sun fesa mata koda ba zata saurara ba.
Kyawawan ‘yammatan buzayen da suketa daukan hankulan jama’a suka jera reras su hudu bayan tashin motarsu aba suka wuce zuwa inda goumar ya ajjiye motar tasa. Hirar suke amma sultana bata fiya sanya musu baki ba,don burinta kawai ta fesarwa goumar abinda yake cikinta.
Akwai takadda guda daya ta sultana da ya tafi karbowa don haka suka dan tsaya suna tattaunawa daga bakin motar tasa kafin ya iso ya bude musu.
Yaro ne da duka duka bazai wuce shekara sha hudu ba ya iso gurin. Fari ne siriri,yana da dan tsaho kadan,yanayin zubin fuskarsa kadai zai shaida maka bafulatanine usul. Sanye yake da wata dakakkiyar shadda sai maiqo takeyi fara qal,kanshi sanye da jar dara sosai irin ta ainihin bare bari. Kana dubansa kasan daga gidan gata ya fito,kuma alamun jikinsa da fatarsa na nuna ainihin jin dadi da yake ciki.
A gabansu ya tsaya yana sallama fuskarsa a sake. Dukkansu suka daga kai suna dubansa,aminata ta amsa masa,sai sultana ta maida kanta tana daidaita qananun litattafan azkar dinta data qarasa debowa daga drawer dinta ta jikin gadonta don bawa ‘yan ss2 da zasu maye gurbinsu damar cin gadonsu da kyau. Gaishesu yayi sannan yace musu
“Wai anason yin magana da wannan” ya fadi yana dan murmushi hadi da nuna sultana da yatsa. Kusan dukkaninsu sai da wuta ta dauke musu na wucin gadi,ba sultana kadai ba,su kansu saida tsoro da fargaba ya cika zukatansu. Suka zuba mata idanu dukkansu,yayin da ita kuma ta zubawa yaron nata idanun ba tare da sanin takamaimai amsar da zata bashi ba.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 37
“wai inji wa?” Najma tayi qarfin halin tambaya da alamun sanyi qwarai cikin muryarta
“My broz….gashican,yace idan ba damuwa zai qaraso…..don Allah aunty ya qaraso din,mun gaji so muke mu aurar dashi mu huta” ya fada yana qyalqyala dariya,da alama akwai sakewa sosai tsakaninsa da wanda ya aikoshi din.
Dukkansu suka maida dubansu inda yaron ya nuna musu. Baiyi qarya ba,matashin saurayine fari tas da yayi zubin buzaye yarensu,saidai su da yake suna shaida duk wani da sukejin harshe daya dashi take suka shaida bafulatanine shima tamkar qaninsa. Yana sanye da shadda da hula sak irin ta qanin nasa,komai nasu irin daya kamar yadda suke kama da juna
“Kaje kace masa matar wani ce” muryar goumar ta ratsa kokwanto da walagigin da zukatansu suka shiga na yadda zasu kaucema wannan kiran.
A birkice ta daga kai tana kallon goumar
“Matar wani?” Ta furta a fili amma a hankali. Juyowa goumar yayi wanda yaji fitar lafazin nata yana duban qwayoyin idanunta kamar yadda ta kafeshi da nata
“Eh….. qarya nayi?” Ya fadi kanshi tsaye yana sake kafeta da kallonsa. Mummunan faduwa gabanta taji yayi. Tsahon kwanakin watannin da kuma shekarun bata taba tuna cewa wai har yanzun itadin matar aliyyu bace,bata sake tuna har yanzun a sunan matar aure take ba,bata sake tuna akwai igiyoyin aurensa guda uku qwarara a kanta ba…..to wai zaman meye takeyi da igiyoyin auren maqiyinta kuma makashinta?,me ta zauna tana yi dasu tsahon shekara hudu?. Kai ta jinjina tana zare kallonta daga kan goumar,taji daci qwarai har saman harshenta,saidai kuma taji dadi da yayi mata tuni da wani muhimmin al’amari da ya kamata ta tuna dashi ta kuma kawo qarshensa cikin rayuwarta gaba daya.
A yanzun ita din wata sultana ce ta daban data fara sanin dadin rayuwa,kyawun rayuwa da kuma cikakken 'yanci da rayuwa ke dashi,tanaso tayi rayuwa kamar kowa,tana so tasan me duniya da rayuwa suka qunsa?,tanason ta fita tayi gwagwarmayar da al'umma zasu amfaneta,dole ta kawo qarshen wannan maqalallun igiyoyi da ko daya bataga amfanin barinsu a sarqafe ba.
Najman ce a gaba dukkansu suna baya su uku,tana iya hango yadda fuskar saurayin ta canza sanda qaninsa ya iskeshi a sanyaye yana labarta masa,batasan ya suka qarke ba,tadai ga yabi bayan motarsu da kallo har suka fice daga makekiyar harabar makarantar.
Cikin motar kanzil bata ce ba,aminata da yasmine sunta hirarsu,goumar da najma da batasan me suke fadi ba suma tasu hirar suke,sai ita daya da suka fari da hannu dafe da gefan kanta tanata zane saman bangon littafin dake cinyarta,wanda ita kanta batasan me take zanawa ba saboda tsabar tunani.
Iska ta shaqa sosai da suka shiga tangamemiyar harabar gidan aba dake garin abuja bayan jirgi ya saukesu a airport. Tadan bi harabar gidan da kallo yadda ya qawatu matuqa da gaske. Sabon gida ne da basu jima da tarewa ba,duka duka sati biyu. Cikin shekarun nan wani irin tumbatsa arziqin aba dama na hamdiyya ABDU ME KANO wato ama keyi,kaman an sake yiwa dukiyarsu yayyafin albarka,mahaukatan kudi kowannensu yake samu. Yanzu haka sun budewa benazeer da batoul manyan manyan boutique cikin garin abuja har guda uku,wanda kowanne kudade ya lasa ba qananu ba,saboda girman boutique din ya kusa wani mini supermarket din B&B BABY DREAM. Komai nasu na dabanne saboda ana sarrafashi ne daga wani kebantaccen kamfani dake sanya tambarin B&B a kowanne kaya,shi yasa kayansu ya fara zama na daban,ya kuma samu karbuwa qwarai da gaske,karbuwar kuma tana da nasaba da yaran da Allah ya hore musu wani irin farinjinin mutane.
Randa sultana tazo wani hutu ta amshi wayar yaran da ama ke musu amfani da ita tana duba account nasu na insta abun ya bata matuqar mamaki. Followers suke dasu masu yawan gaske. Account ne na musamman da ama ta bude kawai saboda yaran,ba abinda take dorawa sai hotunansu. Tun sultana tana kallon pics din har ta gaji saboda yawansu,ta aje wayar kawai tana murmushi
“Kakar zamani” tayi gulmar ama a ranta tana dan dariya qasa qasa.
Motar goumar ya tsayar a farfajiyar ajiyar motoci dake gidan wadda gari ne kusan guda,ya kalli najma
“Samomin wani abu me dan sanyi,ki tahomin da BB(benazeer da batoul)zamu fita dasu wani guri”
“Okay sir” ta fadi tana murmushi sannan ta bude motar ta fice.
“Akwai abinda na riqe miki ne madam?” Goumar ya fadi yana gyara qaramin pillow din dake gefan kujerarsa. Sai data sanya qafafunta waje sannan ta waiwayo
“Goumar” ta kirashi kai tsaye wani irin tsauri na fita daga cikin qwayar idanunta
“Na’am madamme” ya amsa fuskarsa a sake ba komai
“Karka bari ka barar da sauran mutuncin dake tsakaninmu”
“Tofa!,ikon Allah,me kuma nayi?”
“Da batoul da benazeer basu da wani abu a duniya yanzun,kayi qoqari ka daina yi musu tilawar abinda babu wanzuwarsa a duniya……haka nima……ni ba matar kowa bace,ba matar wani bace ni” wata siririyar dariya ya sake mata,ba abinda yake ganowa a idanu da fuskarta sai zallar quruciya da har yanzun shi baiga ta fita kwata kwata a jikinta ba
“Basu da uba a duniya…..ke ba matar kowa bace to kece kika kashe musu uban?” A kaikaice ya waiwaya tana dubansa,maganar tasa ta sake tsaya mata a wuya kamar mulmulallen dutse. Gaba daya abinda ta fahimta goumar kallon shashasha kuma yarinya yakeyi mata,baima dauki maganarta da muhimmanci ba.
“ko ya mutu koma ya rayu wannan duka ba abinda ya shafi sultana bane,abu daya sultana ta sani,bata da wani hadi ko alaqa ta kusa kota nesa dama ko waye” ta fadi da salon tsiwar nan tata data jima bata taba ba
“Ashe dai da sauran bakin har yanzu” goumar ya fada qasa qasa yana dariya sanda take fita a motar. Ta jishi sarai,bata kuma gama fahimtar abinda yake nufi ba,saidai duk da haka ta juyo ta zabga masa harara,ta murguda qaramin bakinta tace
“Baqin ba’abzine,Allah ya qara gwara da Allah ya barka a baqinka” ta buga murfin motar ranta yana suya da ambatar mata sunan maina tana qarawa gaba zuwa cikin gidan cikin sassarfa.
Dariya sosai ya kwashe da ita yana duban hanyar da tabi
“Baki gama laushi ba kenan,hali zanen dutse” ya fada a ransa yana gyada kai gami da ci gaba da dariyarsa sannan ya sanya hannu yana daga glass din motar zuwa sama tare da duban hanyar dawowar najma.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 38
Tunda sukayi maganar nan da goumar walwalarta ta sake daukewa tsaf,duk yadda ta motsa sai zancan goumar ya fado mata a rai
“Matar wani” kalmar data dinga jin nauyinta qwarai,take kuma dugunxuma mata rai. Abun ya tsaye mata qwarai a rai,ashe duk duniya kallon da ake mata kenan?,ita din matar maina Aliyyu ce?. Cikin jikinta ta dinga jin qyamar danganta kanta da matar maina,ta dinga jin ranta da zuciyarta sunqi su yarda da wannan batun.
****K’arfe takwas ne da mintuna na dare, cikin kebantacciyar wajen da aka killace aka kuma zuba masa dining table na alfarma da daukan hankali. Ama ce keta qoqarin serving aba da bibi,wadda tunda tazo bata koma nijer din ba saboda wani likitan gargajiya da take gani cikin kano. Ciwon qafarta ne ya soma matsantawa ama tace ta zauna ayi masa magana,ta fara zuwa kuma alhamdulillah sauqi ya samu,a hakan rigimar komawa nijer takeyi nan da kwanaki masu zuwa.
Magana suke tsakanin aba da bibi, benazeer da batoul nata hawa cinyar bibi su sauka su dane bayan ama. Ba wanda ya damu da zirga zirgar wasansu da sukeyi,sai ama dake qoqarin hanasu wani lokaci gudun kada daya daga cikinsu ya fadi.
“Wadannan ‘yan qaqur din…..wai ina tsohuwarku ne?” Bibi ta fada tana danqo benazeer da kirinkinta ya ninka na batoul,komai nata sak irin na sultana sanda tana qarama,har goumar ya saka mata wani suna wai little sultana
“Tana daki bibi”
“Ni me yarinyar nan keson xama?,anya kuwa kanta qalau?,ace kaine zaman daki ko gajiya bakayi?,ba zaka fito cikin al’ummar muhammadu rasulullahi fa ka zauna ayi tadi dakai?” Bibi ta fada cikin jajjabi.
“Jeki kira uwarku” bibi tace da benazeer tana sakinta. Fuska benazeer din ta kyabe tana duban bibi
“Wai aunty ce uwarmu?”
“Da dawa nake ja’ira?” Dariya ta qyalqyale dashi sannan ta nufi hanyar lobby din da zai kaika dakunansu da gudunta.
Awa guda cur ta kashe akan internet ta system din da ama ta bata kyautar graduation. Bincike kawai takeyi akan abinda ya shafi aikin jarida,haka kawai cikin kwanakin data tsananta addu'ar neman zabin Allah kan makarantar da zata tafi da kuma abinda zata karanta din taji ba abinda yafi kwanta mata a rai irin aikin jaridar. Lokaci guda ta tsinci zuciyarta hankalinta da dukka tunaninta ya karkata ga zama shararriyar 'yar jarida.
Tayi d'ai d'ai a tsakiyar gado,tana sanye da wata maroon abaya,daya daga cikin dressing dinta da tafiyi a yanzu,dankwalin abayar me santsi ne wannan ya sanya ya gaza zama saman lallausar sumarta. Wani qamshi jikinta da dakin dukka yake fiddawa,a yanzun ba abinda ke burgeta sama da turare,komai nata qamshi yakeyi,hatta da abubuwan amfaninta na yau da kullum muddin tana ta'ammali dashi ko da yaushe sai kaji yana wannan sassanyan qamshin nata. Hutu da zama guri daya ya sanya fatarta yin matuqar yin fresh. Gazar gazar din gashin idanunta da na girarta sun sakeyin baqi sidik sun kuma kwanta a fuskarta luf,kamar yadda gefe da gefan fuskarta keda wani irin lafiyayyen kwantaccen gashi me santsi da duhu.
K'ofar taji an murda sannan an budeta da qarfi ta daga fararen idanunta da sukayi laushi saboda kallon allon computer tana duban me shigowar. Idanu ta zubawa yarinyar sanda take shigowa,abinda ya sanyata nutsuwa da shiga taitayinta. Sam bata musu wasa kwata kwata,idan kaga warginsu to suna jikin ama,ko suna tsakanin aba ama bibi ko tanja,wani irin discipline take musu sosai wanda kallo kawai da idanu sun isa su sanyasu shiga taitayinsu.
“Koma kiyi sallama” tace da ita cikin bata fuska da kuma dake rai. Sum sum ta saki qofar ta kuma koma da baya,saiga zazzaqar qaramar muryarta tana jero sallama fes. Amsa mata tayi tana sake qare mata kallo,kullum qara girma sukeyi suna wayo,wayonsu yafi qarfin shekarunsu sosai
“Wai ki fito inji Bibi,za’a yi dinner”
“Ok” tace mata tana gyada kai,sai ta juya tana komawa
“Zonan” ta kirayi benazeer din,haka kawai taji tausayinsu yana saukar mata,hannu ta sanya gefan bedside drawer ta jawota ta fidda wani pink box me cike da chocolates. Tana siyansu ta ajjiye ne kawai saboda su,duk da ba ita da kanta take basu ba,duk sanda tayi niyya kawai tana dauka ta bawa tanja ta basu. Abun yana bawa tanja dariya,itakam ta rasa wannan abu na sultana,anaso ana kaiwa kasuwa?,ko cikakken kallo bata iya yima yaran idan cikin jama’a ne,saidai kuma duk burger banza ce,idan kayi tsinkaye da kyau xaka fahimci dukka motsin yaran bisa idanunta da lurarta yake.
Hannu biyu tasa ta karba da qaramar muryar nan tata tace
“An gode”
“Madalla” ta amsa tana binta da kallo,saita cilla da gudun murna tana fita daga dakin,tana iya jiyota tana qwalawa batoul kira
“B…B” murmushi yadan qwace mata ta girgiza kai,sai kuma a hankali murmushin ya soma bacewa fuskarta,ta miqe da sauri ta shiga toilet ta wanke fuskarta,ta dawo.ta shafa turare kaman yadda ta saba ta daura dankwalinta tana fita daga dakin.
A nutse ta iso wajen,zuwa sannan aba da bibi sun fara cin abincinsu, benazeer da batoul kuma anata faman rikici ama tana sharia,saidai isowar sultana kawai ya sanya suka kama kansu suka hau cin abincin ba tare da sun sake koda tari ba.
Sai datakai har qasa dukkansu tayi musu barka da gida sannan ta miqe taja kujera ta zauna. Da kanta tayi serving kanta,ta fara kai abincin bakinta amma kuma zuciyarta cike fal da tunanin ta inda zata fara sako zancan data quduri aniyar yau din zata fadeshi don a sauke mata nauyin dake bisa kanta ta huta,ta kuma sake cikin tabbaci da yaqinin ba wata alaqa tsakaninta da wani.
Aba ne ya fara gamawa,sai ya koma bawa benazeer da batoul,muddin kuwa ya bawa batoul kafin yazo ga benazeer ta soma rigima,haka ya dinga dariya yana rarraba basu. Yana jin dadin irin wannan yanayin sosai,yaran sun zame musu wani tushe na farinciki da walwalarsu,yaran sun zama tamkar wani budi na alkhairi wa rayuwarsu,tunda aka haifesu al'amura daban daban na alkhairi ke samunsu,komai nasu yana sake bunqasa da ci gaba tamkar dama ragiwar rabonsu yana hannun yaranne sune zasu iso musu dashi. Duk lokacin da ya tuna da haka,ya kuma tuna da yunqurin zubda su da aka soyi a baya sai yayi istigfari. Yaga maganar malamai qarara da suke fadi,kowanne yaro da arziqinsa yake zuwa,hakanan bakasan wanda arziqinka ke a jikinsa ba,hikima ce wannan ta ubangiji.
Sai daya gama da rigimarsu yana goge musu baki sannan yace da sultana
“Kaman naga sanarwar fitowar exam dinku ko?” Kai ta gyada a nutse tana dan ture plate din abincin daga gabanta,duk da ba wani abinci taci me yawa ba
“Eh aba,don fateema Ahmad ta fadamin dazun da safe ta dubo nata”
“to ma sha Allah,Allah yayi jagora,kema sai amanki ko goumar wani ya duba miki naki,tunda sun fini iya shige shigen computer”
“Ama din dai” ta fada qasa qasa yadda ba wanda zai jita,saidai duk da haka ama din ta jita. Ta rasa wanne irin rashin jituwa ne irin haka tsakaninta da goumar din,tana iya kashe wuninta dashi batace masa kanzil ba,shi kuma da yake ya saba a baya abokiyar dabinsa ce to in sha Allah sai ya samu abun tsokanarta,idan taga ya fara sai ta tattara ya nata ya nata tabar masa wajen,takance
“Kaci kanka da kanka”.
“Alhamdulillah,yanzun wanne ecole kike buqatan yi?,kuma wanne cours(course) kike sha’awar yi?” Ajiyar zuciya ta sauke,aba ya soso mata inda yake mata qaiqayi,ya kuma dauko mata mafarin maganar da take juya ta inda zata fara yinta
“journalisme(aikin jarida) shi nake so aba” murmushi aba din yayi,itace mutum ta farko kuma qwaya daya tal a cikin gidan mayak’i data zabi wannan aikin
“To ma sha Allah,saidai kuma munyi magana da bibi,ina kyautata zaton akwai tafiya da zata samemu ni da ama dinku,kuma tafiya ce bata kwana daya ko wata daya ba,tafiya ce ta shekaru biyu ko uku,na samu kujera cikin gwamnatinmu duk da ba’a sanar ba officiellement (a hukumance) ba amma abun tabbatacce ne,so sai a tayamu da addu’a,duk abinda yafi alkhairi Allah ya zabar” kai ta jinjina
“Allah yayi jagora aba ya zaba abinda yafi zama alkhairi”
“Ameen ya rahman” kusan dukansu suka amsa. Shuru yadan ratsa tana ta dan juya hanunta. Cikin qasan ranta takejin kamar abinda zata fadi akwai nauyi,to amma komai nauyinsa abune daya kamata ta tunasar dasu idan sun manta. Dukkan juriyarta da qwarin gwiwarta ta tattaro sannan tace
“Amma aba ina neman alfarma a wajenku” hankalinsa ya bata da kyau da ganin yadda tayi maganar,bama shi ba hatta bibi da ama,saboda baqon abune a wajensu,tun faruwar abun sultanar bata taba neman komai daga wajensu ba
“Ina jinki sultana,fadi duk abinda kk son ki fadi,karkiji komai nidin mahaifi nake a wajenki kuma uba” kai tadan jinjina sannan tace
“Inason a rabani da igiyar auren……ya maina dake kaina” ta danyi dabur dabur wajen furucin saboda yadda furta sunanta kadai yake haifar da wani abu me daci daga saman harshenta.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 39
Dif wuta ta daukewa kowa dake dakin. Tun daga tsakiyar kan ama har tafukan qafafunta sai da taji wani ya tsarga mata,ba wanda ya taba hasashe ko tunanin maganar da zata fada kenan. Kaf cikinsu kowa ya kasa furta komai,kimanin wasu sakanni har sultana ta debe tsammanin wani a cikinsu zaiyi magana sannan aba ya sauke ajiyar zuciya,kafin yace komai bibi ta furta
“Sultana?…..me kike fada haka?” Hannu aba ya dagawa bibi yana kallonta,sai tayi shuru,tsam ama ta miqe ta zagayesu tana barin wajen,saboda batason jin duk wani hukunci da zai fito daga bakin aba,don ta tabbatar zaiyi wahala hukuncin ya dace da abinda ita takeson ji ko son ya kasance
“Kinyi qoqari qwarai sultana da kika iya zama da igiyar auren mutumin da har yau ba wanda yasan inda yake,a raye ko a mace duk ba wanda ya sani,kika raini cikinsa kika haife,kika shiga makaranta kika gama,don yau kin buqaci hakan ba laifi bane,tashi kije zan nemeki in sha Allah,Allah ya yiwa rayuwarki albarka,idan kuma goumar ya shigo ya duba miki sakamakonki”
“To aba,na gode qwarai” ta fadi tana miqewa daga zaman durquson da tayi. Tana shirin juyawa sashen dakunansu suka hada idanu da goumar dake tsaye daga can bakin qofar falon jingine da qofar,hannayensa goye a qirjinsa,da alama kuma yaji komai,don abinda ta gani cikin idanunsa ya karanta mata haka. Harara taso watsa masa amma saita shareshi kaman itama bata ganshi ba ta juya ta wuce lobby.
“Amma dai hamid,kada kacemin ka amshi zancanta da gaske kana nufin yi mata abinda takeso din?” Bibi ta tambayeshi murya qasa qasa tana duban qwayar idanunsa. Ajiyar zuciya ya sauke yana gyara zamansa
“Komai a musulunci bibi yana da iyaka,yana da doka,a shekarun da maina yayi baya nan ba wanda ke da tabbacij yana raye fa,kuma ko a musulunci miji yayi irin wannan bacewar ba tare da ya sake waiwayar matarsa ba ya halatta alqali ya raba auren ayi ma matar GAIBA ta auri wani…..bibi sultana yanzun ba qanqanuwar yarinya bace,ta iya yiwuwa tana da buqatar tayi aure shi yasa ta bijiro da wannan batun da ya kamata ace mu muka fara dubashi” zama tayi sosai tana jifan aba din da wani irin kallo hadi da gatsine fuska
“Hamidou……ka fara kasheni tukunna saika tsinka auren maina kaji”
“Subhanallahi bibi,abun baikai har can ba”
“Ah to,yo Allah na tuba,don qaniyarta nawa take duka duka da har za’a ce waiko tana da buqatar aure?, ina cewa kwata kwata sha tara shekarun nata suke?,to ko labarin mutuwar maina aka samu ai bata isa tayi wani auren ba sai tayi masa idda”
“Ya maina ma yana raye……” Goumar ya fada
“………in sha Allah,jikina yana bani haka” ya qarasa fadi ganin dukka sun waiwayo sun zuba masa idanu,sai ya sauke hannayensa yana ci gaba da takowa cikin falon
“Bazamuyi masa fatan mutuwa ba aba baiga jininsa ba diyoyinsa,kai din ubane,a duk inda yake kaci gaba da yi masa addu’a Allah ya bayyanashi,ko kuma ubangiji ya karkato da hankalinsa gida” shuru sukayi su dukka jikinsu a a mace,saidai maganganun goumar dake cike da nutsuwa da kuma hankali sun ratsasu.
Tunda ta shiga daki take nanata kowacce kalma data fita a bakinta,saida zuciyarta ta gamsar da ita bata aikata wani abu me muni ba,hakanan batayi amfani da tsauraran kalamai ba wajen bayyana musu yankewar igiyar aurensu takeso,hannu ta daga tana addu'a Allah yasa aba ya yanke hukunci da wurwuri,ta yadda zata samu cikakken 'yanci kamar kowacce mace,tayi karatunta iya yadda takeso ta kuma gamsu.
Agogo ta dinga dubawa har sai data tabbatar da lokacin da goumar yake zama babban falon ama shi dasu benazeer su cikawa mutane kunne da karadi,sai ta dauki hijabinta ta sanya saman kayan baccinta donta gama shirin kwanciya,kasancewar bata fiya kaiwa dare can can batayi bacci ba.
Takardunta ta diba ta sanya loppy tana fita a dakin. Yau din sabanin kullum ne,zaka samesu ko yaushe sun cika falon da hayaniya da wasanninsu,amma a yau din sai ta samu yaran duka sunyi bacci zube a tsakiyar ama da goumar din. Daga goumar din kuma har ama idanunsu na bisa tv.
Motsinta ya sanya ama da goumar din juyowa duk suna kallonta. Idanun goumar bai sanyata jin komai ba,amma sai idanun ama taji sunyi mata mugun nauyi. Ta dinga jin kamar ana dabaibayeta,cikin gangar jikinta ta dinga jinta kamar me laifin da aka tsare.
Miqewar ama din kafin ta iso tana daukar benazeer ya sanya ta dan sake ji wani iri tana cewa
“Tanja zata zo ta dauki batoul,sai da safe”
“Allah ya bamu Alkhairi ama” ta fada a kunyace
“Ameen sultana” yadda ta amsa matan a sake sai ya rage mata tsarguwar da tayi,ta samu waje ta zauna tana duban fuskar batoul dake bacci. Bakinta gaje gaje da chocolate,tasan kuma ba aikin kowa bane sai na goumar,shi yasa yaran kullum qara habaka suke suna qiba mul mul abinsu,duk wanda ya gansu saiya tanka,wannan ya sanya duk sati ama ke sanyawa ana sauke musu qur’ani.
Hannu ta sanya ta shafi cute face din batoul tana dauke mata gashin daya warware daga band din kanta don suma sunyo gadon gashi me tsaho da santsi irin na iyaye da kakanni
“Ah waima,unuhunn……wai a haka fa sonta kikeyi ko?,bayan kin gama kashe musu uba da baki,kina kuma neman a sakeki” goumar da bakinsa baya shuru muddin shi da sultana ne ya fadi. Miskilin gaske ne a zahiri da fuska,amma indai shi da sultana ne dama tun tale tale sun saba. Idanuwa ta dago ta zabga masa hararar da bata samu daman sakar masa ba dazu
“Wai kai meye yayi maka zafi da shiga sha’anina ne baqin buzu?”
“Fadi ki sake fadi,baqin buzu nake me farar aniya da zuciya”
“A hakan?,kaga ma ni ba wannan bane ya kawoni,don bani da lokacin wannan maganar,aba ne yace idan ka shigo ka dubamin exam dina”
“Zan duba miki yanzun kuwa,don ni din me jin maganar magabatansa ne……exam kuma dai saidai a cirota a ajjiye don ba inda zaki sake tafiya,sanda akeson kiyi karatun bakiyi ba sai yanzun da kike matar wani?” Ya fadi kansa tsaye ba tare da damuwa da abinda zataji ba yana sanya hannu ya dauko laptop dinsa dake ajiye a gefansa wadda bai jima da gama aiki da ita ba.
Tsam ta miqe,ba goumar ba,har wajen da take zaune a kansa sai da taji ta tsanesa. Hawaye fal idanunta tana dubansa dishi dishi,tana shirya kalaman da zata gaya masa da zata fanshe wannan maganganun da ya yaba mata,abu biyu ta iya gaya masa taji muryarta ta soma rawa,saita juya bata ida gaya masan ba,tana jinsa yana cewa ta kawo takardun ya cika aikin aba,ko waiwayoshi batayi ba bare ta saurareshi. Ko a jikinsa yaci gaba da aikinsa yana dariya qasa qasa cikin ransa hadi da cije lips dinsa na qasa.
Tun daga lokacin bata sake bi ta kansa ba,bata kuma sake bari sun hada koda hanya cikin gidan ba bare mazauni,rainon maina ne,tasan kuma zai aikata abinda yafi hakan,duk zuciyar tasu iri daya ce ta gayawa kanta,shi yasa ta yanke hukuncin nesanta qwarai dashi.
Aba ne da kansa ya kirata ya miqa mata hard copy na result dinta. Sanda ta karba hawaye ne ya kwance mata,ta samu fiye da marks din da ta tsammaci zata samu,ta cinye kowanne subject,abinda tayi hasashen zata samu ta samu fiye da hakan,ta kifa takardun saman fuskarta tana kiran sunan Allah,yau sultana ita keda wannan result din da abaya kaf gidansu koda cikin mafarki ba wanda ya taba kawo mata kwatankwacinsa saboda zallar qiyayyarta da karatu.
Ba ama ba hatta aba abun ya faranta masa rai matuqa da gaske,bai kuma yi sanya ba ya bata option ta zabi duk kalar kyautar da takeso yayi mata,ya bata dogon takarda yace ta rubuta list. Hannunta rawa ya dinga yi,ta kasa rubuta komai,sai daga bisani cikin rawar bakin bayan ama ta matsa mata ta rubuta din tace
“Umra nakeso aba”
“Sau nawa?” Hawaye ya biyo kuncinta tana tuna adadin zuwanta,sau uku ne,amma saidai duk sanda taje din tana cikin rudu,tana asalin sultanarta,batasan muhimmancin wajen ba,batasan kuma dimbin falala da wajen yake dashi ba,taje ne kawai taji dadin jirgi,ta kuma shaqata a kantunan dake daura da harami,tasha chocolate laban da ice cream har sau babu adadi. Amma a yanzun da tasan muhimmanci da girman wajen sai shauqinsa yaketa kamata,yanzun da ilimi ya ratsata burinta kawai shine zuwa wajen sau babu adadi cikin rayuwarta
“Sau nawa kikeson xuwa?” Aba ya tambayeta
“Sau babu adadi” ta qarasa fadi tana rushewa da kuka
“Kin samu in sha Allah” ya fadi yana nufin hakan har cikin zuciyarsa kuwa. Diyar mohmoud ce tafi qarfin komai,uwa uba ya samu sanyin idaniyarsa halittu mafi soyuwa a gareshi da silarta BENAZEER DA BATOUL. A arziqin da Allah yayi masa inda ana zuwa kullum kuma tana da buqatar zuwa din zai iya kaita.
Ya mata alqawarin muddin yana raye din zata yita zuwa har sai sanda tace ta gaji. Ita kuwa tasan zata yita zuwa kenan muddin ranta,muddin akwai wadata wa aba,akwai lafiya cikin jikinta,saboda bata tunanin akwai ranar da zatazo tace ta gaji da zuwa wannan gurin.
*. *. **. Randa bibi zata juya nijer sai taji haka kawai tana sha’awar zuwa. Tare suka tafin,da harda goumar ta kafe indai tare zasuyi tafiyar ita ta fasa,dole yayi gaba daga baya aba ya basu driver da escort uku.
Sosai taji dadin xuwa nijer,ta ji har cikin ranta lallai a gida take,abu daya ke yawan takurata,duk sanda ta gilma wani guri da tasha dabdala a baya,ko guraren da maina yafi yawan zama sai taji duk walwalar da take ciki ta gushe,wannan ya sanya ta dinga kame kanta daga shiga wasu guraren,ciki harda nahiyar dakunan dake sassan bibi wanda anan me akkuwa ta auku.
Wata guda ta shafe a nijer,daidai lokacin kuma muqamin aba ya tabbata,tafiya ta tabbata daga nijer to nijeria har zuwa qasar FRANCE!.
TOFA MASU KARATU,DAB MUKE DA ISA GURIN😄,muna dab da mu qarasa gurin da na tabbatar kowa ya qagauta a isa
FRANCE……NEW CHAPTER UNLOCKED🥰
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 40
FRANCE (PARIS)
Charles de Gaulle Airport
Avenue champs elysees
8th arrondissements
Cikin awa daya da saukesu da jirgin qatar airways yayi a airport din Charles de Gaulle suka iso champ elysees avenue. Unguwar dake da matuqar kyau tsari da kuma dadin zama,wadda take dauke da dukkan nau'ikan shop shop,malls restaurant da coffee shops harda makarantu. Unguwa ce me kyau qwarai da dadin rayuwa,wannan ta sanya aba ya zaba musu zama a cikinta. Cikin daya daga cikin apartment dake unguwar wanda gwamnatin nijer ta bashi.
Babban apartment ne dake qunshe da dakunan bacci guda hudu,biyu ta gaban gidan inda zaka bulla har balcony zuwa harabar gidan, biyu kuma ta cikin gidan wanda suke hade da backyard na gidan. Kowa yasan ginin bature gini ne me matuqar kyau da daukan hankali,komai na gidan a tsare yake a kuma killace,sun iso cikin gidan bisa jagorancin wakilan qasar nijer a nan din da suka tarbesu a hukumance,suka yiwa aba duk wata tarba data kamata.
Karfe hudu agogon paris suna cikin gidan,sun gama zagaya ko ina da duba ko ina. Sultana kam da ido take bin komai tana sake tabbatar da maganar hausawa da suke cewa tafiya mabudin ilimi,tun daga abuja zuwa gidan da suke ciki a yanzun take ganin mabanbantan al'amura. Benazeer da batoul kam sai tsalle tsallensu sukeyi,suna biye da ama duk inda ta sanya qafarta. Walwalar yaran data qaru kawai ta sanyawa ama farinciki,tana ji a ranta zaiyi wuya tabar qasar nan nan kusa,har sai yaran sun samu kalar ilimin da take musu kwadayin samu. Tanason su fita daban,su zama na musamman,kamar yadda gatan da suke samu ya banbanta da gatan duk wani d'iya dake familyn MAYAK'I,kamar kuma yadda suka zamo jikokin farko a wajensu aba din.
A nutse ta taka izuwa babban curtains daya suturta babbar qofar glass na dakin da zai iya baka daman ganin cikin unguwar da kuma duk wanda ke zirga zirga ta street din nasu. Qofar ta murda ta fita zuwa balcony din,sassanyan yanayi na la'asar sakaliya dake gauraye da qamshin tsirrai da suka wadaci unguwar ya daki fuskarta,iskar ta shiga sosai cikin hancinta ta isa hunhunta ta sauketa a nutse tana kuma fidda wata me zafi. Ajiyar zuciya ta sauke,tana fatan taji ruhi da zuciyarta ta nutsu amma. Ta lumshe fararen kewayayyun idanunta da suke da wani irin qwalli kamar an diga mai a cikinsu,haka kawai taji bugun zuciyarta yana dan sauyawa a hankali yana qara gudu. Da hanzari ta ware idanun nata cikin mamakin abinda ya haifar mata da hakan,sai ta aza hannun nata saman qirjin nata tana qoqarin controlling sabon yanayin data tsinci kanta a ciki.
Tsahon wasu mintuna babu sauyi,sake maida idanunta tayi zata lumshe karadin benazeer ya cika mata kunnuwa
“Aunty……aunty kinga” hannayenta ta sauke tana waiwayowa zuwa ga yarinyar. Da gudunta take nufarta tana nuna nata wata qatotuwar teddy. Murmushi ta saki dan siriri tana tuna rayuwarta,yadda tayi yayin tara teddy kaman hauka,batajin cikinsu ma akwai wanda zai qaunaci teddy din yadda ta sota
“Kizo inji ama” benazeer ta sake fadi tanata qoqarin ganin ta goya Teddy din,sai kuma ta juya da gudu gudu tana sauka hadi da kiran
“B…..B” Juyawa tayi tana komawa cikin dakinta ta dauki mayafin gown din jikinta ta yafa tana bin bayansu.
Daga qofar dakin da ama ke ciki din ta tsaya saboda rashin ganin dacewar shigarta dakin,don daki ne da ama ta zabawa aba,duk da cewa aba dinma baya nan ya fita tare da mutanen da suka yo masa rakiya zuwa nan din.
Knocking tayi ama dake ciki tace ta shigo. Hakanan cikin jin nauyi ta murda qofar dakin tana shiga. Babban dakine da yafi kowanne girma da kyan furniture,aman tana tsaye da wani folder a hannunta tana dubawa,ta amsa sallamar tana kallon sultana sannan ta miqa mata takardun tana cewa
“Ba hutu,ba zama,sun kusa gama daukar dalibai,aba yace ki duba,cikin universities din wacce ce tsarinsu yayi miki?”
“Allah sarki ubana na kaina” ta fada hawaye yana cika idanunta. Hannu biyu tasa ta karba tana kallon folder din. Itakam dai kawai tayi rashin mahaifinta hamani ne,amma zata iya cewa iyayenta sun maye mata gurbinsa har fiye da haka,batasan wani abu waishi maraici ba,bata taba ji ko ganin zumunci irin nasu ba,tasan indai ana batun dacewa da family itakam ta dace
“Amma ki kula ki duba location na kowacce university ki zabi wadda ba zaki dinga shan doguwar tafiya ba”
“In sha Allah ama”. Ta fadi farinciki yana cika zuciyarta fal,burinta ya kusa cika na zama ‘yar jarida,ta rungume folder din tana fita daga dakin.
Tsabar zumudi ya hanata tsaiwa ta kintsa dakin ta zauna duba jami'o'in,tanayi tana browsing a wayarta da babu layi a ciki duk kuwa da tsadar wayar,akwai wifi da suka samu a gidan don haka bata buqatar komai don research din.
Har tanja ta gama abinda ya dace tayi ta biyo ta dakin tana nade tsakiyar gado tana aikin canki canki. Cikin zolaya tanja tace
“Wai sultee kamar yanzu zaki fara zuwa makaranta a rayuwarki,wannan zumudi haka?,xuwa makarantar ma kamar yafi komai yi miki dadi” tashi tayi ta zauna tana yatsina fuska saboda yadda bayanta ya riqe sakamakon rub da cikin da tayi na kusan awa daya tana cewa
“Ji nakeyi kamar yanzu aka haifeni tanja,kaman yanzu ne na soma rayuwa,ai da can ba rayuwa nakeyi ba tanja,rayuwar da babu ilimi a ciki?,meye marabarka da gawa?”
“Irin wannan lokacin maina yakeson gani,shi yayita burin gani tattare da ke,ya Allahu ko ina wannan bawa naka ya shiga?” Qwaqwwaran motsi sultana batayi ba,sai tayi kaman bataji abinda tanja tace ba,inda sunsan adadin dimuwa da qyamatar da ruhinta ke yiwa sunansa kawai bama shi din kansa ba…….da babu wanda zaiyi kuskuren sake kiran sunansa a gabanta
“Bari na kintsa miki wajen kafin ki gama” a hankali ta motsa labbanta tace
“To” tana maida hankalinta ga wayarta cikin tsananin nutsuwa,yayin da zuciyarta taci gaba da motsa da wani irin sautin tsana da qiyayya duk sanda kunnuwanta suka tuna mata sautin kiran sunansa da tanja tayi.
Satinsu daya suka gama huce gajiya,sai ama ta fara diban jikokinta suna fita shan iska. Kullum da inda zasu,sai idan sun dawo kaji labari cakwai a bakin benazeer,don ba kasafai batoul ke da surutu haka ba. Hasalima ita saita nema debo dabi’un abbanta sak da sak,tana da wani irin miskilanci da kuma basarwa. Haka kawai idan taso saita tashi da ‘yan shirun, benazeer tayi hirar duniya taqi kulata,idan taga haka tasan tana nufin yau ba zasuyi wasa ba ko ifce ifcensu da suka saba ba sai tahau tsokanarta,ba kuwa zata qyaleta ba har sai ta sakata kuka,sau tari sai ama ta shiga tsakani,ko kuma idan suka cikawa sultana kunne ta leqo shikenan sai benazeer din tayi laqwas ta shiga taitayinta.
A irin wannan lokacin ama kan zauna kawai tana binsu da kallo, zuciyarta tana mata haske tana kuma mata fari,wani lokaci kuma damuwa ta cika zuciyarta,dukkansu su biyun sun dauko attitude na mutum biyu ne, benazeer sak SULTANA tana yarinya,batoul kuwa MAINA ce har yabar gabansu.
Duk da garine dake da ababen kallo sosai,gari ne dake da ababen sha’awa amma ita bata sha’awar fita ko ina. Zaman kadaicin da taketa yi ya sanyata karance karance a matsayinta na wadda keson fadawa harkar karatun jarida,a hankali har abun ya zame mata jiki. A nan taga wata makarantar koyar da girke girke na qasashe daban daban,koda ta duba kudin registration din sai taga yayi yawa,don haka ta maida site din ta rufe bata sake budeshi ba. Ranar ama ta karba aron ipad dinta taga ta soma register,ta fahimci yawan kudin ya hanata qarasawa. Murmushi ama tayi,sultana….. sultana,akwai barin kashi a ciki,ba zata taba bude baki tace ga matsala ko damuwarta ba,sai ta shiga site din ta qarasa komai ta biya kuma kudaden,sai gayawa sultana tayi ranar da zata fara zuwa.
Nauyi da kunyar ama suka sake kamata,tana kunyar yadda ta azama kanta dukkan nauyinta,komai nata itace,bata qyashin kashe mata ko nawa ne, ba’a maganar su benazeer da suke fuskantar wani irin gata,idan akace gata ana nufin gata na qarshe,irin gatan da ake kwatance dashi. Komai nasu me tsada ne,komai nasu kuma na musamman ne,hatta kuwa da brush da zasu wanke haqoransu. Amma kuma duk da gatan da ake gwada musu hakan bai sanya sunyi lako lako da tarbiyyarsu ba. Sosai suke samun kulawa da tarbiyya,don ama da kanta take koya musu qur’ani. Da yake sunyi gadon kwanya,sai gashi da qananun shekarunsu sunyi nisa a alqur’ani,hadda kuma tartilan cikin qwaqwalensu. Ta siya musu kayan karatu kala kala da zasu taimaka musu, harshensu kuma ya fara juyewa da qira’ar sheik imam khusari.
Makaranta me kyau aba ya duba ya sakasu,inda suke karatu da dukka harasa biyun, French da English harda qarin larabci.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA.
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 41
Cikin watanni biyu aba yayi settling komai ta fara zuwa makaranta. Qaramar mota ya siya mata daidai d'iya mace,ta kaita makarantar koyon tuqin mota ya zube kudi ta koyi tuqi da kyau suka bata license. Hakan ya mata dadi qwarai,don ta huta da tafiya railway ko kiran taxi.
Shigarta makarantar ya sake sanya idanunta suka bude da rayuwa,ta qara sanin mece duniya?,tarin al'umma mabanbanta masu mabanbantan halaye da dabi'u. Ta sake sanin tabbas duniya tana da girma da fadi,taga kalolin tarbiyya iri iri al'adau dabi'u da kuma halaye,wanda kusan kullum idan ta dawo sai ta bawa ama labari. Murmushi kawai ama keyi,itama sai yanzu take sake tabbatar da quruciyarta,lallai a baya in banda quruciya da tabara babu abinda sultanan ta sani. Duk da haka suna biye kuma suna kula da ita,ko don girman igiyoyin dake saman kanta,wanda tun wancan lokacin da bibi tayi magana ba'a sake tada zancan ba.
Suna exam semester farko aba ya ajjiye musu visa dinsu na zuwa umra. Ranar kasa bacci sultana tayi. Hakanan Allah ya jarabceta da son zuwa madina da makka,tun daga sanda ilimin addininta ya fara zurfi ta fahimci muhimmancin gurin gaba daya zuciyarta ta tafi can.
Washegari goumar ya dira a Paris,sai a sannan tasan dashi za'a yi tafiyar. A sannan tana parlor tana duba wasu litattafai nata door bell tayi qara,tanja ta bude masa ya shigo riqe da jakarsa. Daga benazeer har batoul yarda abun wasan hannunsu sukayi sukayi kansa kamar zasu shide saboda murna,shi kuwa ya tattarasu duk da girmansu ya dagasu yana zagaye dasu.
Har suka gama abinsu tana zaune bata daga kai ba,sai da suka nutsu suka zauna tanja ta ajjiye masa drinks da snacks tana gaya masa ama tana bandaki,sai ta fara tattare litattafanta da zummar barin wajen idanunta na kallon litattafan nata tace dashi
“Ina yini,kana lafiya?”
Gwanin tsokana baya fasa halinsa,tabe baki yayi yana cewa
“Nidai ban roqi gaisuwa ba bare a wulaqantani ehe,meye wani ina yini kana lafiya?” Tsaiwa tayi da abinda takeyi ta xuba mishi fararen idanunta, kwanyarta na mata tariyar tarin kamanceceniyar halayya dai da uban dakinsa sarkin zalunci da mugunta wato maina kaman yadda ta rada masa
“Kaidai ba’a iya maka wallahi,Allah ya sawwaqe” saita dauki kayayyakinta a hannu tana yin gaba
“Ya kyauta mana gaba daya,mutum se shegen qunci da dacin rai kamar wanda aka kashewa diyan fari” ya qarasa fada yana galla mata harara. Tasan halin goumar,baiqi su kwana sunayi ba,don haka ko waiwayoshi batayi ba ta shige dakinta,amma ranta cike fal dashi,tana kuma tunanin hanyar da zata bi ta taka masa burki,yadda yake shige mata sharafi ya soma isarta hakanan.
Bata qara bari sun gamu ba sai ranar da zasu wuce. Tafiyar tasu dukkansu ce,harda tanja,amma sai ya zamana duk cikinsu sultana din tafi zumudi saboda a wajenta tamkar zuwan farko ne.
Tafiyar awanni tara bayan yada zango a wani qasar Wizz Air Malta ya saukesu a filin tashi da saukar jiragen sama dake garin madina don can suka fara sauka. Wata ajiyar zuciya me qarfi ta sauke kamar wadda aka finciki zuciyarta. Ta furzar da iska daga bakinta tana jin daukin ganinta cikin masallacin ma'aiki. Daga wankansu cin abincinsu a masaukinsu zuwa fitowarsu masallacin duk sai taji kaman basa sauri,ji take kamar duk duniya ita daya keda buqata,kamar duk duniya ita keda damuwa a qirjinta,kamar kowa baya da matsala sai ita kadai. Tana ganinta a raudha kuwa kuka ta saki sosai,saidai qasan ranta taji nutsuwa tana saukar mata,wannan ya taimaka ta samu nutsuwa tayi addu'a sosai.
Dukka kwanakin da sukayi a madina babu wanda bata amfaneshi ba da tarin addu'o'in da ita kanta batasan adadinsa ba. Sai gata a yau wai itace da yiwa ummanta NAFESSA da mahaifinta HAMANI addu'ar samun rahamar ubangiji,lallai hankali da nutsuwa ya samu,madalla da wannan rayuwa data samu sauyinta.
Randa suka sauka a garin makka kuwa kayanta kawai ta ajjiye tayi wanka ta fice,ko ama su benazeer ta barwa sallahu su gaya mata ita ta wuce harami. Ta kasa nutsuwa don masaukin nasu daga nan idan ta bude window din dakinsu tana gano harami sosai,saita dinga ji kamar ana fusgarta.
Sanda suka fito ma ita ta bace cikin masallacin,don haka ama ta fara tata ibadar, benazeer da batoul ma sukayi nasu waje,wanda ama batasan ma ina sukaje ba sai da suka dawo hannu dumu dumu da siyayyan kayan zaqi,tunda kafin su fita dama already aba ya basu kudi a hannunsu.
Da rigima suka dawo,mutuniyar batoul tayi kicin kicin da fuska tana harara benazeer,tambayar duniya taqi bayani sai ice cream da ta saka a gaba,ita kuwa benazeer ba abinda ya shafeta ta zauna ta bude abinta ta fara sha tana dariya. Da kallo ama ta bita,sak yadda sultana ke cakar da yara zamanin quruciyarta da shegen tsokana da yiwa yara dariya. Daqyar ama ta lallasota ta gaya mata
“Mutane take kulawa ama,sai kuma tayita basu labari mu ‘yan nijer nigeria da paris ne” waiwayawa aman tayi tana duban benazeer,suna hada idanu jikin benazeer din yayi sanyi saboda tasan kalar wannan kallon na ama
“Bana hanaki dogon surutu irin haka ba benazeer?,kina so na saka wuqa na rage miki tsahon bakinki?” Da sauri ta girgiza kai idanunta na hada hawaye
“To daga yau na hana,idan zakuje siyan abu kuje ku dawo,ba ruwanku da kowa kina jina?” Kai ta gyada mata tana lanqwashe qafafunta taci gaba da shan sanyinta. Dariya taso qwacewa ama,wato tsoratar da itan da tayin bazai hanata qarasa shan kayanta ba
“Gado ba karambani ba” ta furta can qasa tana sake tuna mata da sultana da qananun shekarunta cikin qasar nijer mansion house na MAYAK’I family.
Da wata irin kasala mutuwar jiki data zuciya rungume da dardumarta take fitowa daga masallacin. Idanunta sun tasa sun kuma yi jaa saboda yawan kukan da tayi a gaban ka’aba. Rabin kanta sarawa yakeyi saboda abincin da bataci ba wunin yau din gaba daya sai zam zam data dinga sha sosai kaman ba gobe.
Sanye da baqar jallabiyya yake takawa a farfajiyar wajen. Tsahonsa bayananne ne,hakanan nannadaddiyar sumarsa.
Bata lura dashi ba kamar yadda shima din da alama bai lura da ita ba yana cikin gaggawa ne,wannan yayi sanadin da saura kadan kafadunsu su hade waje guda,abinda ya sanya sultana janyewa gefe zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu saboda qamshin turarennan da hancinta ya shaqa qwarai da gaske fiye da yadda take jiyo qamshin daga nesa a mabanbantan gurare……….qamshin yaja hankalinta ta waiga a hargitse tana duban wanda ya giftata din……..
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 42
Rufewar da idanunta sukayi,da kuma irin bugun da zuciyarta keyi ya sanya idanunta suka nuna mata shi a matsayin maina,daga bisani kuma a hankali ganinta ya washe,ainihin kamanninsa suka fito mata
“Sannu ko?,yi haquri don Allah” ya fada yana daga Mata hannu da sassauqar muryarsa dake bayyana zallar sauqin kansa,ya bata haqurinne da hausa kawai don baya tsammanin ko kadan zataji me zaya fada,don kuwa koda alama batayi masa kama da launin jinsin hausawa ba. Kanta ne yayi wani mummunar sarawa,sai data sake matsawa nesa kadan dashi sannan ta gyada kai tana furta
“Ba komai” a wahale sannan ta juya da sasarfa tana barin gurin,don ko kusa bata qaunar sheqar qamshin wannan bala’e’en turaren
“Uhmm……nace ba,don Allah ko zan iya sanin masaukinku?” Taji ya fadi a bayanta bayan ta baro wajen sosai,don tayi tsammanin ma inda suka tsaya din daga nan ba lallai ka hangoshi ba. Muryar tasa ta sanyata waiwayowa sai suka hada ido. Kai ta girgiza masa alamun a’ah,sai ya marairaice yana ci gaba da binta
“Don Allah,kada kice a’ah” hannuwanta dukka ta sanya tana dage doguwar rigarta tana kuma qarawa qafafunta karsashin yin sauri,don burinta ta tsere masa daga wajen. Ba abinda yake sake hadsasawa zuciyarta sai wani irin bugawa
“Please” ya sake fadi ba tare daya dakata da binta ba
“Ka daina bina,nan din waje ne me alfarma”
“Na sani,ni dinma alkhairi nake nufinki dashi,bata yadda zan miki magana a nan kuma zuciyata sharri ne a cikinta game dake”
“Na gamaka da girman gurin da wanda ake bautawa a wajen ma dakata” ta sake fada daidai sanda ta hangi goumar yana nufo wajen,yana riqe da hannun BATOUL tana bashi labari,shima kuma da alama dukka hankalinsa yana kan batoul,saidai hango sultana da wani na biye da ita ya sanyashi dauke dukka hankalinsa a kan yarinyar ya maido kansu batoul.
Bata fasa sassarfar tsere masa idanunta nakan fuskar Goumar data tabbatar sai yayi mata shishshigi,kaman yadda bai fasa binta yana mata magiya ba,hakanan goumar bai fasa nufosu ba fuskarsa da idanunsa na nuna wani irin emotion.
Ta karanci abinda ke fuskar Goumar,kaman ma a fusace yake ainun,yau kam sai tayi maganinsa taga idan akwai abinda zai iya,don haka suna zuwa dab dashi ta dakata,ta kuma karantawa matashin Address na hotel harda number dakinta
“Na gode sosai,sunana suhail kefa?”
“Sultana” ta fadi a taqaice tana juyawa ta rabe goumar ta wuce.
Sai data fara nisa da gurin suhail ya maida dubansa ga goumar da yayi tsam ya zuba masa wannan idanun nasu me matuqar kwarjini da haiba irin na maina,idanun buzaye dake da wani irin sirri da kuma launi na daban.
A idanu suhail yaga suna kamanceceniya da sultana,saidai shi din baqi ne sosai kuwa akan kalar fatar sultana dake jazur kamar ta fito daha yankin larabawa,wannan kama da ya gani yasa ya miqa masa hannu yana fadin
“Assalamualaikum” girman kalmar da sanin ma’anarta kadai ya hana goumar qin miqa masa hannu. Ya bashi hannun,saidai kuma ya bar masa saqo yana fadin
“Ita din matar wani ne,kada kayi gangancin shiga gonar da ba taka bace,kada kuma kayi yunqurin keta dokar Allah” sosai sai jikin suhail yayi sanyi,amma a yadda karo daya yake jinta cikin kowanne sassa na zuciyarta daga kallon farko,sai yaji kalaman goumar basu shigeshi ba
“Ni jikina sam bai bani haka ba,idan ma kai din rival ne saidai nace maka kayi haquri na riga na kamu,ma’assalama” ya fada yana yin gaba.
Tun daga ranar sai goumar ya dauke mata wuta tsaf,ta daina ganin koda haqoransa,itakam hakan yafi mata dadi,don dama so take ya fita a sabgarta kuma ya fita din,takance a ranta
“Aikin banza aikin wofi,koshi wanda kakeyin abun saboda shi bai isheni kallo ba,bai kuma isa yace zai damu rayuwata ba bare kai”
Suhail kuwa tasha ganinshi a hanya ko cikin masaukin nasu da alama ita yake nema,saita bace masa kota koma har sai yabar wajen. A daidai lokacin lokacin ubangijinta kawai take dashi,ita kanta cikin zuciyarta taji nutsuwa da gamsuwar lallai tayi ibada iya yadda ubangiji ya bata iko,fatanta kawai ta zama karbabba,muddin kuwa ta karbun tayi imanin zata cimma dukkan nasara da kyautatuwar rayuwa.
Sati uku sukayi suka koma Paris ta rungumi karatunta,wanda babu abinda take gani sai budi da nasara,duk wani nasibi da budi data roqo akan karatunta tana ganinsa,karatun tamkar ana buda kwanyarta ana zuba mata shi,nan da nan kafin ma su kammala ajin farko sunanta ya fara yin fice cikin makarantar tsakanin dubban dalibai dake department dinsu.
Duk yadda takai ga janye jikinta da rashin son jama’a sai Allah ya bata farinjini sosai cikin makarantar,kowa ta zauna dashi dai ya qaunaceta,duk da miskilancinta bata iya wulaqanci ba sam,sannu sannu sai gashi ta fara dan sakewa da jama’a. Koda ba zatayi mu’amala dakai ba amma zata maka murmushi saman fuskarta,wannan sai ya sake zama abun burgewar jama’a a wajenta.
Tun wannan zuwan da sukayi sai zuwa umrar ya zame musu tamkar jiki kamar yadda aba yayi mata alqawari. Abun sai ya zama kaman ya tsara musu kanshi da kanshi,duk sanda suka samu hutun makaranta ita dasu benazeer to a saudiyya suke yin abinsu,suyi wata guda suna ibada sannan su dawo kuma a soma shirye shiryen komawa bakin karatu.
Ta riqi karatunta gam da matuqar muhimmanci,tana bashi dukkan lokacinta,saidai kuma hakan bai hanata ibada ko koyon wasu abubuwa da suka shafi rayuwa ba wandada tasan tana da naqasu ta bangaren,kaman koyon girke girke,hanyoyin kula da kai da kuma gyara kai da wata balarabiyar oman ke koya musu. Macace me baiwar sanin ilimin halittar diya mace,shiga ajin matar ya faranta mata ainun,don ya sake maidata wata irin ‘yar gayu….. mace me aji,irin macen kuma da tasan kanta ciki da waje. Sai a sannan ta karanci ama cikin hikima. Wato ita ama ba’a banza ba ta fita daban a zuciyar aba,duk da cewa aure qaddarar wasu mazajen ce,to amma bata tunanin tana cikin qaddarar aba,wasu abubuwan ma da yadda take kula da rayuwarta da kuma kanta dukka sai yanzu hankali da ya game sultanan take karantarta,wasu abubuwan tayi qoqarin daukesu,wasu kuma su bata kunya.
Abinda bata sani ba ama din ta fita zurfin nazari sanya idanu da qwaqwqwafi,tuni ta fahimci sultana,sai bata nuna mata ba,amma itama saita sakata a nata ajin na yadda mace zata amsa sunanta mace a idanun mata ‘yan uwanta dama maza abokan cudayyarta. Ta sake salute na ama,ba banza ba ta sake fita daban da faccalolinta,tun tale tale komai na ama dabanne,she’s so classy,har kuma a yanzun dabi’arnan tana nan,shekaru da fara zuwan girma bai sanya ta canza ba.
Ta zame mata mentor sosai ta fanni da dama,ita kadai data kalla ya sake sanya mata sha’awar koyon girke girke iri daban daban. Ama din kamar half cast za’a kirata,uwa uba kuma ita din tayi zaman qasashe tun zamanin quruciya har zuwa yau,wannan ya sanya ta iya nau’ikan abinciccika kala daban daban,kuma da kadan da kadan sai da sultana da iya da yawa daga cikinsu.
KOMAI NISAN DARE gari zai waye
Cikin babban dakin taron dake mallakin makarantar,cike yake da dalibai irinsu sultana dake murnar amsar sakamakonsu na kammala karatun aikin jarida fanni daban daban,sai kuma manyan baqi iyaye da ‘yan uwan daliban dake qasashe da kuma garuruwa daban daban cikin paris da wajenta.
Tana sanye da academic regalia data dora saman wani tattausan lace da ya lashe kudade masu ciwo da ama ta siya mata,ta kuma bayar akayi masa dinki me aji. Lite make-up ne a fuskarta wanda zaka iya rantsuwa da Allah ba komai saman fuskarta saboda nutsuwa da kwanciyar da kwalliyar tayi a saman fuskartata.
Tun daga takalmin qafarta har zuwa mini handbag da medium mayafinta idan akayi lissafi a qalla zasu tada jari me qarfi ga wani. Komai nata me sanyi da tsari,kaman yadda halittar ta take da daukan hankali da saukar da wani irin nutsuwa.
Siririn kwallin da aka sanya ma fararen qwayoyin idanunta da kuma red lipstick da ta shafa ya fidda mata wata haiba da kwarjini na musamman.
Tana zaune a inda aka tanada saboda dalibai,amma gaba daya hankalinta yana kan batoul da benazeer da aka yiwa kwalliya sosai cikin wata red gown da tayi masiiiifar kwanciya a lafiyayyar fatarsu da hutu da gata ya jiqa sosai. Sai kai kawo sukeyi suna ‘yan guje gujensu tsakanin mutane,duk kuma inda zasu gifta din sai sunja hankulan mutane. Wasu su jasu suyi hotuna,wasu su basu qananun gift da ba’a raba baturen mutum dasu.
Kiransun da aka fara yi daya bayan daya ya sanya dole ta haqura da lura da kai kawonsu,duk da tasan idanun aba ama goumar harma da bibi da tayi tattaki tun daga nijer domin ganin yadda gudaliyar tata a yau zata karbi sakamakon da zai bayyanata a cikakkiyar ‘yar jarida.
Sanda sunanta ya fita a cikin mic haka ta miqe tana ratsa mutane,kunya gami da nauyin idanuwan da sukayo kanta dukka suka cikata,haka ta dinga takawa cike da nutsuwa har takai saman step din da kowanne dalibi ke tsaiwa tana qasqantar da ganinta.
Idanu sosai takeji cikin jikinta tamkar yawansu ya wuce yawan adadin jama’ar dake wajen kadai. Bayan gajeriyar gabatarwar dake nuna da qwazo da nagartarta,kwanya da kaifin ganewa da take dashi,da kuma kasancewarta daya daga cikin dalibai guda biyar da sukafi kowanne dalibi samun high mark. Ji ta dinga ji kamar zata fadi a wajen,gaba daya qafafunta sunyi laushi hawaye ya cika idanunta. A kowanne bigire na rayuwa data tsaya ba abinda take gani sai haske,wani irin budi take gani a duk matakin karatun data taka,batasan abinda ke nufi da hakan a gareta ba,me yiwuwa akwai hukimar ubangiji da ya sanya qiyayyar karatu me yawa a ranta a baya.
Kuyi haquri dai,ku qara haquri,naso yau na kaiku inda ya kamata aje din,amma yau da gobe ta riqeni,duk da haka ku bini bashi gobe in sha Allah,na gode sosai.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 43
Hannu ta sanya ta amshi certificate dinta,wanda tayi tsammanin bayan ta karba din zata koma ta zauna ne kamar kowanne dalibi......amma kuma a'ah. Kyaututtuka na karramawa ne suka yita fitowa saboda qoqarin data nuna da hazaqa a guraren da suka danyi ayyuka dasu na neman qwarewa watannin da suka wuce da kuma cikin makarantar kanta,kasancewar su mutanene masu girmama mutum irinta,sunason suga mutum me talent qwarai da gaske. Sai ta dinga ji kamar tarihi yana maimaita kansa a hassan Ibrahim gwarzo makarantar da har yau take kewarta,take kuma jin tamkar ta koma can. Makarantar ta zame mata wani mabudi,ta kuma zamewa rayuwarta haske kuma fitila dan jagorarta daga duhu izuwa haske.
Kafin a kammala taron duka ta bata fuskarta da koke koke,sai tissue da ama keta bata tana goge fuskar saboda hotuna da aketason dauka da ita,musamman su benazeer da suka ja hankulan mutane qwarai.
Tana duqe tana qoqarin controlling hawayenta muryar benazeer ta karade hall din ta cikin mic. Da zazzaqar muryarta tayi sallama,sallamar data sanya kowa dake wajen murmusawa,ta kuma saka sultana dagowa da sauri. Tayi dare dare saman step din tana murmushi,cikin yaren france da ya kama harshenta matuqa da gaske tamkar yaren hausa da suke magana dashi yau da gobe a gida ta soma magana
“Ina gaida aunty na…..ina gaida mommy na ama…. oncle goumar….kaka na aba…..sai daddy na…….daddy na ina gaisheka……muna kewarka daddy,yaushe zamu ganka?” Ta qarashe fada muryarta tana raunana.
Tafi wajen ya dauka,yayin da maganar ta doki qirjin duk wani ahalin mayak'i dake a wajen. Sultana kam maida bayanta tayi makarin kujera ta jinginar tana rufe idanunta, qirjinta yana bugawa kusa da kusa. Goumar ya riga ya gama yiwa tunaninsu lahani,ya gama cusa musu wannan tunanin na mahaifinsu wanda batasan yaushe zaibar zukatansu ba.
Kusan jikinta a sanyaye aka kammala taron,saidai dab da za'a kammala din saiga sanarwa daga wani gidan tv kai tsaye suke neman sultana zuwa channel dinsu zatayi interview,suka bata date wanda ya dauki makonni kusan hudu,dai dai da sanda suka kammala wasu gyare gyare na shirye shiryen da suke gabatarwa a channel din nasu. Wannan shine abinda ya wanke mata zuciyarta,farinciki ya kamata sosai,abinda bata taba tunani ba,yau ita sultana wani tashan talbijin dake a qasar turawa ke nemanta da kansu?
“Alhamdulillah” kawai ta dinga maimaitawa tana jin farinciki yana ratsata,ko ta ina addu’arta ke karbuwa,cikin qaramin lokaci buri da muradinta ke dab da cika.
Koda suka koma gida bacci tayi sosai na gajiya,bata tashi ba sai azahar,tana yin sallah ta sake komawa,don duka kwanakin zirga zirga sukeyi don tabbatuwar taron. Bayan sallar la'asar benazeer ta shigo,ta bita da kallon harara sannan ta zaunar da ita. Data fara yi mata fada akan abinda tayi dazun saita sakar mata kuka,abinda ya sanyata sakin baki kawai tana kallonta,sannan kuma cikin bacin rai tace
“Oho…..tun bankai ga dukanki ba?,hala duka kike buqata ko?” Kai ta girgiza tana share hawayen fuskarta
“We missed him mommy,uncle goumar yace yana nan amma bamu taba ganinsa ba,sai a hoto ya taba nuna mana shi sau daya” gabanta yayi mummunar faduwa,da gaske goumar yakeyi bazai bar shiga shirginta ba?,wato har wani nuni yake musu dashi a hoto
“Tashi ki bani waje” ta fada tana watsa mata harara. Har ta miqe sai ta dawo a sanyaye,ta tsugunna gabanta murya a sanyaye
“Kiyi haquri aunty” ta fadi tana mutsuka idanunta da qwalla ke fita. Ido tadan xuba mata na sakanni,tausayinsu su dukka yana ratsata,ita da yaran gaba dayansu ababen tausayi ne,sai itama taji nata idanun sun ciko,ta sanya hannu ta jawota ta rungumeta a jikinta.
Ajiyar zuciya yarinyar ta saki tana yin luf a jikin nata,kasancewar basu fiya samun wannan damar ba,saida tayo controlling nata hawayen don kada ta gani sannan ta sake tana cewa
“Kije wajen bibi naji kaman tanja na kiranki”
“To” ta amsa tana miqewa da dan tsallenta tamkar komai bai faru ba,gashinta dake daure yanaya lilo a bayanta ta fice a dakin.
Binta tayi da kallo har zuwa bakin qofar,sai a sannan taga ama dake tsaye hannayenta goye a qirjinta. Sauke hannuwan tayi ta tako cikin dakin,yau dai sau daya tak taji zata yima.sultana din magana,zafin qiyayyar aliyyu da take gani a idanunta sun fara bata tsoro,tayi tsammanin ilimi shekaru da kuma wayewa sata samu zasu goge komai,koda komai din bai gogu ba tayi zaton xai ragu ainun har ya zamana bai iya bayyanuwa a idanun mutane
“Sai yaushe sultana?,sai yaushe zaki sassautama ranki wannan abun dake qulle cikun zuciyarki?” Karon farko tayi mata tambayar ido cikin ido.
Qasa tayi da kanta,ba zata iya jurar kallon qwayar idanun ama ba,nauyin da dukka ruhi keji akan uwa game da d'anta ya saukar mata. Da alama abun ya zafafi ama a yau tunda har ta magantu,shine abinda sultana ta raya a ranta,kamar ta karanci abinda take rayawar sai ta bata amsa tana gyara zamanta
“Kada ki dauka naji haushi ne ko nayi fushi ko kuma zanyi fushin,ko kadan,shekarun da muka dauka abinda nake gani cikin idanunki na saba ganin irinsun……amma yanzun rayuwa tana sauyawa ne,yaranki yaran aliyyu ne,bai kamata kina bari suna karantar wannan harshness din dake cikin idanuwa da kalamanki ba,wani abun bau cancanci ‘ya’ya suna sani akan iyayensu ba,wata kakkaifa kuma qaqqarfar dangantaka ne da tafi qarfin kowa yayi shishshigi a cikinta………zamu je umra cikin satinnan in sha Allah,daga can zamu wuce nijer sai bayan bikin aminata da yasmine zamu dawo,amma immediately saboda maganar gidan tv dincan” kai ta gyada hawaye suna son sauko mata,amma batason tayi kukan,kada ama ta zaci don ta mata fada ne
“Kiyi haquri” tace da ama bayan aman ta miqe,a sanyaye ta waiwayo tana dubanta
“Ke ya cancanci ayita bawa haquri sultana,ba za’a daki mutum a hanashi kuka ba,kawai dai kukan saffa saffa ya dace kayi,tunda kayi imanin ko meye ya sameka ko zai sameka daga Allah ne” kai ta sake kadawa a sanyaye.
Hannuwanta dukka biyun ta sanya ta lullube fuskarta dasu tana sakin wani asirtaccen kuka. Ita kanta ciwon da qirjinta ke mata a kullum ta tuna da ita din wacece ya soma isarta,bataso,tanaso ta rayu da zuciya sakakkiya kamar kowa,ta rasa me yasa ta kasa watsar da komai,ta manta da komai?,ta manta da wanzuwarsa a duniya kamar yadda yayi nesa da rayuwarsu itama ta nesanta kanta da komai da yashafeshi
“In sha Allah wannan zai zama jigon addu’a ta a wannan tafiyar……in sha Allah zan gayawa ubangiji na……zan roqeshi da dukkan sunan da yake amsa addu’a idan an kirashi da su,zan masa magiya ya sake nesantaka daga cikin tunani……daga cikin rayuwata ni da ‘ya’yana……zan roqi ubangiji ya kawo silar tsinkewar igiyarka data daureni” ta yiwa kanta wadannan alqawuran.
Tana takawa zuwa dakinta amma tunani ne fal zuciyarta. Duk da rakinta da ake gani.....duk da qin yarda da daukan qaddarar da wasu ke gani kaman ta gaza JARUMA ce sultanar,zama da igiyar wani da bakaso tsahon shekaru babban nauyi ne,ya kamata susan abunyi akai......amma wai ina maina?,INA MAINA YA SHIGA?,YANA RAYE KUWA ANYA?. Da wannan tunanin kadai saida zuciyarta ta buga,idan har ya mutu a ina?,a hannun wa?,waye ya sururta d'anta?.
M A I N A
Wani irin matsakaicin falo ne dake da wani irin atmosphere mai matuqar daukan hankali da tafiya da tunani. Komai dake wajen tun daga color da yanayin da aka tsarashi da kuma unguwar da ainihin ginin ma yake zakasan ya banbanta ya kuma yi nisa qwarai da kalar tamu rayuwar.
Cikin daya daga cikin luxury sofas dake zagaye da falon yake zaune sosai,irin zaman da zakasan lallai yayi relaxing yadda ya kamata,bashi kuma da nufin tashi yanxu,hakanan da alama ba wani schedule dake a gabansa.
Zabgegen farin ba'abzine,jazur tamkar ka sanya yatsa jini ya fito,dogo me murjajjen jiki,ma'abocin baqar sassalkar suma,tun daga saman kanshi,girarshi,gashin idanunsa har zuwa kumatunsa da aka yiwa sumar wani irin gyara dake zamewa fuskar mazaje ado na musamman me kama da gold a inda akasan daraja da kimarsa.
Yanayin kayan dake jikinsa pajamas ne masu gajeran wando da kuma gajeran hannu,farare tassss tasu masu tsananin taushi da aka saqasu daga audiga mafi tsada da daraja. Dogoyan fararen qafafuwansa da hannayensa dukka lullube suke da gargasa baqa sidik saidai duk yawan gargasar bata hana bayyanuwar murdewa damtse da qafafunsa ba da kuma tsananin da fatarsa ke dashi wanda ke cakude da sirkin ja......duk da a zaune yake structure na jikinsa ya fita sosai a matsayin mutum ma'abicin shiga gym da daga qarafuna.
Babu gilmawar annuri ko kadan saman fuskarsa,hannunsa na dauke da tab dinsa,a nutse kuma yana bin hotunan daya bayan daya yana kalla.
A duniya bai taba jarabtuwa da soyayyar wani abu da baisan asalinsa ko tushensa ba irin yadda ya jarabtu da soyayyar wadannan twins din ba,a duk sanda yake kallon hotunan yaran yakanji tamkar ya cirosu daga jikin hotunan ya gansu a zahiri,yakanji har a ransa soyayyar d'ansa da goumar ya gaya masa sultana ta haifa tana hauhawa a ransa,yaron da ya tabbatar da gangan goumar yaqi bari ya gansa tsahon shekarun,duk wata jafa ko hanya da zaiga yaron goumar din ya tosheta,ya gaya masa.muddin yanasin ganinsa ya dawo gida,ya dawo cikin ahalinsa ya fuskanci ko ma meye. Abinda ya tabbatar goumar bazai fahimta ba a sannan,duk bayanin da zaiwa goumar bazai fahimceshi ba,shi daya yasan meke faruwa dashi,shi daya zai iya fahimtar damuwar da matsalar. Ya zuwa yanzun yana jin haqurinsa ya gaza...... tafiyarsan nan ta qarshe da ta zama cikamakin burikansa tazo masa da abubuwan ban mamaki masu tarin yawa,mafarkinsa yakai ga gaci,ya cimma nasarar rayuwar da a mafarki bai taba tunanin zata isar masa ba......yanajin yakai qarshe,ya kuma tuqe......yana da buqatar yayi gaba da gaba da ahalinsa......ya shirya karbar kowanne hukunci,ya kuma shirya fuskantar su dukka gaba daya. Yanason ganin d'ansa.....yana da buqatar ya bayyanawa d'ansa shi waye a wajensa,amma kuma dukka wadannan abubuwan me ya tanada?.
“Ina da rabb” ya bawa kansa amsa,saboda yayi imani shi daya yasan me yake cikin zuciyarsa,shi daya yasan gwagwarmayar da ya fada shi daya yasan yadd ya rayu ya kawo wadannan shekarun har ya qarasa zama CIKAKKEN MUTUM ya fita a cikakken DR MAINA.
Shawara guda daya tak zuciyarsa ta bashi yaji farinciki da gamsuwa. Yaji a ransa tabbas mafitarsa kenan,ya dangane da dakin Allah yakai masa kukansa kamar yadda ya saba,a wannan karon ya nemi qwarin gwiwar tunkarar ahalinsa,ya nemi jarumtar iya karbar kowanne hukunci da mahaifansa zasu yanke masa
“Harda hukuncin rabuwa da sultana?” Mummunan tunanin da yaso birkitashi ya darsu a zuciyarsa lokaci guda.
Kai ya dinga girgiza da sauri da sauri yana jin kowanne sashe na jikinsa na qaryata yiwuwar karbar hakan. Ya aza dukka qarfinsa ya tankwabe tunanin gefe,ya tattara hankalinsa akan sabon hotunan yaran.
Murmushi ya dinga saki yana binsu da kallo gami da saukesu daya bayan daya akan tab din kamar yadda ya saba. Yana da hotunansu bila adadin dashi kansa baisan yawansu ba,abinda ya sani dai ba’a taba dora wani hoto nasu a personal Instagram account din yaran bai saukeshi ba. Yayi bincike yayi bincike amma ya kasa fahimtar ‘yan wanne qasa ne?,ina ne asalinsu?, ba’a taba dora hoton wani abu ko hoton wani ba sai nasu,ba wani abu da aka tana dorawa da zai sanyaka fahimtar su din su waye.
Sai daya gama saukesu tsaf sannan ya sauya wallpaper na iPhone da tab dinsa da sabon hoton nasu kaman yadda ya saba. Tsaiwa yayi yana kallon yadda hoton yayi kyau saman screen din wayar tasa,wani miskilin murmushi ya kubce masa.
Mutanen da suke mu’amala dashi wansunsu da yawa suna tsammanin yaran ‘yan uwansa ne,banda sunsan single yake da yawa zasu zaci nasa ne yaran saboda yawan hotunansu da yake dasu,da kuma yawan dorasun da yakeyi zaman dukka screen nasa da yake using dashi. Wasu lokutan shi kansa yakan gayawa kansa ya zaqe da yawa,to amma shi kansa baisan me yasa yake jinsu har cikin jininsa ba.
Knocking da akayi a qofar falon dake waje hade da kada bell ya sanyashi daga kansa,ko ba’a yi magana ko ya duba camera ba yasan waye,ba wanda ke hada masa irin wannan rubdugun knocking da bell din idan ba suhail ba,sai ya aje tab din ya miqe zuwa bakin qofar.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 44
Yana bude masa qofar ya dawo ciki abinsa ya koma inda ya tashi ya zauna. Suhail din ya shigo kunnensa manne da waya yana amsawa. Hannun kujera ya samu ya zauna yana ci gaba da amsa wayar,yayin da maina ke sake ci gaba da kallon fuskokin yaran.
“Haka Allah yake jarabtar bayinsa da qaunar wasu bayin nasa na daban da basusan da zamanka ba” suhail ya fada yana danna wayarsa. A nutse maina ya daga kai yana duban fuskar suhail cike da mamakin furucinsa. Yaune karon farko da yayi magana akan yaran cikin kwantar da harshe da kuma murya. Kusan ko yaushe yafi zabar tsokanarsa da yi masa iya shegen
“Mutumina gwara kayi aure ka haife mana twins dinnan ko fuskokin yaran nan zasu huta” sau tari saidai yayi murmushi kawai ya shafi sumarsa. Har yanzu cikin suhail da ahmad bello da sukewa laqabi da sardauna…..mutanen da suka zame masa shaqiqai kuma makusanta bayan barinsa gida basu taba sanin ya taba aure harda yaro ba.
Wani irin mutum ne shi tun asali me tsananin zurfin ciki,zaiyi wahala kaji qorafi ko wani zance daban a bakinsa. Tun a halittarshi yana da qaranta magana da surutu......a yanzun kuma sai abun ya zame masa ninki.
Akwai yawa yawan mutane da sukayi tsammanin kurma ne shi din,rana ta farko kuma da yayi magana a gabansu a mamakance suke waiwayowa suna dubanshi saboda ranar ne suka fara jin lafazin bakinshi.
Kallon da maina din yakewa suhail ya tabbatar tambaya ce cikin idanun nasa,amma yasan zaiyi wahala ya tambayeshin kai tsaye,don haka ya aza wayar saman qawataccen glass table din gabansa ya goye hannayensa a qirji yana duban idanun mainan
“Na fada soyayya da kallo daya tak aliyyu……I don’t know how to explain it….abun kamar shirin film,ganina daya tak da ita ta ban kuma ganinta ba,har yanzu ban mance fuskarta da kuma kamanninta ba…..ina jinta kusa da zuciyata qwarai,bazan kuma fasa nemanta ba a duk inda nake tunanin zan ganta”.
Kamar maina ya samu statue haka ya zuba masa idanunshi har ya kammala,suhail din ya fuskanci hakan,yasan halin mutumin qwarai da gaske,ba lallai ya fahimci dukka dogon bayanin nan nasa ba,don haka yaja dan qaramin tsaki yana daukar wayarsa
“Bansan me yasa na zauna naketa maka bayani ba bayan zuciyarka ba’a halicceta don taso diya mace har tayi sha’awar aure ba…….abu daya naga kana yiwa mahaukacin so wadannan yaran da bakasan nahiyar ma da suke ba” ya qarashe maganar yana zuba idanunsa kan wayarsa. Maganar tasa ta sanya maina maida dubansa saman fuskar tab dinsa,sannan ya zame tab din ya ajjiye yana hade hannayensa guri guda
“Me yasa ka yiwa zuciyata wannan fassarar?” Ya jefawa suhail tambayar da wani irin sound me taushi saidai kuma cikin tsakiyar taushin muryar tasa akwai wani irin deep amo me saurin isar da saqo kunnen me saurarensa koda baka shirya hakan ba.
Sai da suhail ya waiwayo ya kalleshi sannan yace
“Ah….. Mr man,nayi qarya ne?,ko iya yadda LAILAH keyi maka tsahon shekaru inajin ya kamata zuciyarka ta narke ka saurareta……amma fa banga alama ba,ba alamun zakayi giving up,ko kunyar sardauna baka ji?” Kai kawai ya kada yana kallon gefansa
“Akwai abubuwa da yawa da baki bazai iya bayaninsu ba suhail…….”
“I see” ya maida masa cikin gatse,sai kuma ya tsaya cak yana sake duban maina
“Kai…….if i can remember kamar naga face din yaran nan zuwa na umra last fa?” A nutse maina ya sake kallonsa ba tare da ya motsa ko yace komai ba,saidai cikin qasa da second biyu ya fahimci ba wasa bane irin na suhail,da gaske yake
“Really?” Ya tambayeshi yana dage dukka girarshi biyun
“Yes…..da gaske nake…..kaman a hannun rival dinnan da kaji ina bawa sardauna labari…..a harami ne tabbas” haka kawai ajiyar zuciyar da maina baisan dalilinta ba ta kufce masa,muryarsa so cool yace
“Zuciyata gaba daya ta karkata zuwa umra,ka dubamin yadda zan samu ticket da wuri mana please”
“Kai da ka fini xuwa akai akai ai kaman ka fini sanin masu siyan ticket da wuri ko?”
“Baya nan man din…..baya kusa” ya amsa mishi da alamun zaquwa sosai cikin muryarsa,sannan shigowar Moses wanda ya fito daga kitchen dauke da breakfast tray na ogan nashi yaja hanakalinsu.
Rusunawa yayi ya gaida suhail,suhail din ya amsa masa yana dan janshi da tsokana kadan sannan moses din ya wuce yana shirya dining
“Amma zuwa nayi muji yaushe sardauna zai dawo,mu kammala lissafi saboda nasan kowa yana da nashi plan din ko?”
“Bazan zauna jiran sardauna ba…….kuyi komai koda bananan ba matsala bane,tunda idan na dawo dinma duka duka bazan haura sati daya ba zan wuce paris……next month asibitin zai fara aiki in sha Allah”
“Alright……ba matsala” suhail ya fadi yana lalubar wata number
“Kwana nawa zakayi?” Idanunsa na a rufe,yatsansa guda daya ya dagawa suhail sannan labbansa suka motsa da
“Month”. Sai ya maida kansa ga dannar wayar,ya sani duk sanda maina ya shiga irin wannan mode din bai fiyason takura ko yawan magana ba,wannan ya sanya suke dauke masa qafa da kuma yi masa uzuri,duk da basusan taqamaimen damuwarsa ba har kwanan yau.
****Benazeer da batoul ke akan gaba janye da wasu kyawawan qananun qawatattun luggage dai dai su wanda ama ta bada order yinsu musamman saboda benazeer da batoul din tun daga dubai. Kowanne luggage na dauke da sunayensu a jiki da wani ruwan gold din rubutu. Abayar jikinsu ma haka ta kasance,gray color ce da tayi masifar dacewa da yanayin yaran. Kubul kubul dasu babu rama babu mummunar qiba,hutu jin dadi da zallar nutsuwa ta bayyana tattare dasu. Komai dake a jikin dayar akwai jikin dayar,abinda zai matuqar rudar dame kallonsu yayi tsammanin mutum daya ne aka tsagashi gida biyu,don hatta da rufaffen takalmin dake qafarsu na kamfanin D&G ba abinda ya banbantasu dana juna,haka siririn agogon gold dake hannuwansu.
Suna gaba ama da sultana na biye dasu,su dinma abayar ce a jikinsu me matuqar tsada da daukan hankula.
Batasan me ya sanya ba wannan karon tunda suka diro madeena gabbanta suke a sanyaye,tayita neman tsari daga sharrin shaidan koda shike da niyyar hanata ibada wannan karon tuquru kaman yadda ta saba,tunda shi din maqiyin duk wani dan adam ne,ta sanya hannunta ta gyara zaman glass dinta dake taimakawa ganinta,wanda akayi mata tun a wancan lokacin da idanunta suka samu raunin gani. Tun zuwansu Austria ama ta sanya aka sabunta mata shi,aka maidashi na ado sosai,a wancan lokacin qin yin amfani tayi dashi,sai a sannu data fara fahimtar inda rayuwarta ta sanya gaba ta nemeshi,ya zuwa yanzun kuwa tana nan dasu kala kala,dukkansu zaka dauka tana sakasu ne saboda ado.
Ba yadda aba baiyi da ita ya fiddata a duba idanun ayi mata aiki me kyau ba amma ta qiya,tsoro takeji qwarai,tana ganin idan aka tabata ana iya rasa idanun duka ma.
Kamar ko yaushe suna isa masauki tayi wanka taci abinci ta wuce masallaci,tayita zuba idanun ganinsu benazeer da batoul amma bata gansu ba,har ta kammala ta dawo bata gansu ba.
Samunsu tayi cikin dakin sun baje kayan ciye ciye sunata fama,benazeer tafi batoul bawa abun muhimmanci,ita batoul da alama ta gama ta koma kan waya.
Harara ta watsa musu dukkansu sai suka nutsu,bata ce musu komai ba har tashiga ta sake wanka ta fito,sai ta samu dakin wayam da alama sun gudu wajen ama,ta gyada kai tana jan qwafa ta koma saman gado ta nade ta fidda wayarta tana dan duba wasu abubuwa da suka shafi channel din da take sanya ran farawa aiki tare da dakon jiran shigowarsu. A qalla yanzun sun fara girma,shekara hudu cikin ta biyar ai sun san gabas sunsan yamma,ba zata barsu haka siddan su dinga zuwa waje me alfarma irin wannan ba tare da sunsan muhimmancinsa ba. Har ta gama jiran bacci ya saceta basu dawo ba,basu hadu ba sai data tashi sallar asuba,sai data kammala tata sallar sannan ta tashesu sukayi tasu,ta ritsasu tana tambayarsu me ya zaunar dasu jiya?.
Inda inda suka fara mata,daga qarshe batoul ta sanya kuka, benazeer ce me bada haquri,ta musu kashedi sosai,wanda tana tsaka da yin ama ta shigo.
Dariya ta dinga yi ciki ciki,ita tunda take bata taba ganin alaqar uwa da d'a irin ta sultana ba,gaba daya ta zame musu wata senior master bawai mummy ba. Da ama tabi ba'asi sultana ta gaya mata,sai ama taqi bin bayansu
“Eh da gaskiyar auntynmu,daga yau a dinga qoqarin zuwa masjid kunji ko?,amma kuma auty ayi mana afuwa,a dinga tafiya daga baya zamu taho tunda munsan wajen kuma bamu da nisa,munyi alqawarin ba zamu sake zama daki ba,idan kuma mukace mun gaji a barmu mu dawo daki mu huta” ama ta fada tana hada hannayenta waje guda. Murmushi ne ya subucewa sultana hadi da nauyin ama,saita kada kai kawai,ama dai ta samu ta kwashe ‘yan jikokinta suka fice hawaye shabe shabe.
Tun daga ranar kuwa basu saba alqawari ba,kamar wasu manyan 'yammata,koda ta tafi zasu biyo bayanta,saidai kuma sai sun gama qailularsu,siye siyen chocolate da fadace fadacensu na tsakanin sako da sako.
Satinsu guda kacal bibi itama ta iso,sukayi jiranta ta gama nata ibadar suka wuce makka.
makka
Al_ajyad street
SWISSOTEL HOTEL MAKKA
Kai tsaye motar kamfanin dake da alhakin tarbarsa ta wuce dashi swissotel,wanda kusan duk sanda ya shigo garin makka din bashi da hotel din da ya wuce wannan,hotel ne da yake jin dadin zama cikinsa sosai,saboda daga nan yana iya hangen haram tarwai,har wasu lokuta idan yayi tsaye daga bakin window din dakinsa yakan yi addu’o’i sosai kafin ya sake labule ya wuce.
VIp suite suka bashi saboda cancantarsa da cab din,aka tabbatar da shigar da jakarsa ciki,da kuma tambayar abinda yake da buqata suka gabatar masa sannan suka danqa masa dakin a hannunsa.
A nutse yake cire lallausar rigar saman kayan jikinsa,daya daga cikin shigar ‘yan qasar hindu,riga ce me wando da top dinta qarama me budadden gaba,wadda an saqata ne da yadin zaren vicuna mai matuqar daraja da tsada. Da baya ya zauna saman sofa din dake dakin yana lumshe idanunsa,kanshi yana kallon sama yana furzar da numfashi da kadan da kadan ta cikin bakinsa da wata iska me zafi.
Wata nutsuwa ke zagayashi,a duk sanda ya tsinci kansa cikin qasar sai ya dinga jin zuciya da qirjinsa wasai,saidai kuma hakan baya hanashi jin wani abu a jikinsa,irin jin da me nauyin laifi saman kansa yakanji a duk sanda ya gujewa laifinsa da ya aikata. Tsahon shekaru yana jin wannan abun a dukka wani motsi ko tattaki na rayuwarsa,ko sau daya koda na minti daya zuciya ruhi da kuma gangar jikinsa basu taba samun hutu ba game da hakan,a haka ya rayu…….darare da yawa bacci yana qauracewa idanunsa……lokutta da yawa yana sarayar da baccinsa ya zauna dangwargwar,sautukanta……furucinta da lafazzanta suna dawo masa sabbi fil cikin kansa….. zuciyarsa na tuhumarsa,tana sake maimaita tuhumrsa,me yasa?……don me ya gaza kai zuciyarsa nesa?,don me yasa ya kasa haquri ya dauke kai?,me yasa ta gaza cin albarkacin nafessa?,ya cika alqawari?,yayi abinda ya dace?,a yau inda nafessa zata dawo duniya zaya iya fuskantarta?. Bai sani ba shima…..baisan me yahau kansa ba,baisan me ya fusgeshi ba……kawai yaji har cikin ransa ya aikata,hakan kima shine dai dai…..shi zai sanyata nutsuwa,shi zai zama mafarin lanqwasuwarta da shigarta taitayinta. To ashe dukka yayi bahaguwar fahimta,ashe muqulli ya sanya zai kuma bude musu sabbin shafuka da qofofin qaddara masau tsauri da nisan zango irin wannan.
Sai daya samu nutsuwa gabbansa suka huta sannan ya bude idanun nasa yana duban agogon dake manne a bango, mintuna qalilan suka rage a tayar da sallar isha’i,kuma yana da matuqar muradin samun sallar cikin jam’i,kamar yadda duk tsanani ko wuya ko a ina yake baya barin jam’in kowacce sallah ya WUCESHI,musamman asuba da isha’i saboda falala dake cikinsu.
Kayan jikinsa ya fara ragewa,yana cirewar yana jin yadda wayarsa ke qugi. Baiyi koda attempting din tabata ba,saboda yaga wacece me kiran,yasan kuma ba Wanda ya shaida mata ya tabo nan din sai suhail,yanzun kuma ba lokacin wasa ko lokacin bata lokaci bane,duk da dama can ya bawa wajen muhimmanci me tarin yawa cikin rayuwarsa,da har baya iya daukan lokaci baizo ba,to amma yanzun buqatu gareshi masu nauyi,wani babban aiki ne a gabansa da yake da buqatar jajircewa yayi addu’a da kyau.
Cikin kayansa ya fidda bathrobe ya rataya sannan ya wuce toilet abinsa.
A gaggauce suka iso swissotel suka kuma gama komai suka karba maqullan dakuna guda biyu kamar yadda suka saba,daya na ama da aba,daya kuma nata da su benazeer da bibi,don haka classic room suka dauka me gadaje uku.
Suna shiga ta duba lokaci,sannan ta sake duba babban agogon nan dake garin makka. Lokacin isha’i ya kusa yi,don haka a gaggauce ta cire kayanta don watsa ruwa,tanason a qalla takai tsakiyar dare gaban ka’aba,akwai tarin buqatu da take dasu,ta kuma tabbatar tayi imani tare da yaqinin amsasu a wajen kamar yankan wuqa yake,ba wata addu’a da tayi bataga karbuwarta ba,a yanxun ma tazo da kukan yankewar igiyar aure da tayi saura tsakaninta da maina,don bata da qwarin gwiwar sake fuskantar su aba da zan can. Tun tana kasa kunnuwa taji aba din ya nemeta harta fidda rai,kullum zancan yana a ranta,saboda xuwa yanzun tasan girma da nauyin igiyar dake kanta tsahon shekarun……..
“Ku gama abinda kukeyi da wuri,da minti goma yau zan rigaku fita” ta fada tana daga musu yatsunta gami da shigewa toilet din,sai bibi ta bita da kallo tana kama baki,abun mamaki wai yau sultana ce da tsantseni da tsananta tarbiyya
“Yar nema,kina kamarsu ma sanda kike zuwa daki kike kwance abinki har muje mu dawo kina bacci shine yanzun da wanan sirisirin hannuwan naki kike irga musu lokaci” qaramar dariya ta saki tana tsaka da brush,don fes taji abinda bibin ta fada. Itakam ta karanceta irin mutanen dake son jikoki da yayan jikoki ne fiye ma da yadda sukewa yaransu da suka haifa soyayya
“Allah yabar mana ke bibi” ta fada qasa qasa tana tuna wasu lokuta na quruciyarta can shekarun baya murmushi ya sake subuce mata
“Ba abinda bashi da iyaka sai ikon Allah” ta fadi a ranta
KACIBUS……….😂INJI HAUSAWA DON BANA QARASA BA,SAI NACE KUZO MUJE 🏃🏽♀️🏃🏽♀️
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 44
Yana bude masa qofar ya dawo ciki abinsa ya koma inda ya tashi ya zauna. Suhail din ya shigo kunnensa manne da waya yana amsawa. Hannun kujera ya samu ya zauna yana ci gaba da amsa wayar,yayin da maina ke sake ci gaba da kallon fuskokin yaran.
“Haka Allah yake jarabtar bayinsa da qaunar wasu bayin nasa na daban da basusan da zamanka ba” suhail ya fada yana danna wayarsa. A nutse maina ya daga kai yana duban fuskar suhail cike da mamakin furucinsa. Yaune karon farko da yayi magana akan yaran cikin kwantar da harshe da kuma murya. Kusan ko yaushe yafi zabar tsokanarsa da yi masa iya shegen
“Mutumina gwara kayi aure ka haife mana twins dinnan ko fuskokin yaran nan zasu huta” sau tari saidai yayi murmushi kawai ya shafi sumarsa. Har yanzu cikin suhail da ahmad bello da sukewa laqabi da sardauna…..mutanen da suka zame masa shaqiqai kuma makusanta bayan barinsa gida basu taba sanin ya taba aure harda yaro ba.
Wani irin mutum ne shi tun asali me tsananin zurfin ciki,zaiyi wahala kaji qorafi ko wani zance daban a bakinsa. Tun a halittarshi yana da qaranta magana da surutu......a yanzun kuma sai abun ya zame masa ninki.
Akwai yawa yawan mutane da sukayi tsammanin kurma ne shi din,rana ta farko kuma da yayi magana a gabansu a mamakance suke waiwayowa suna dubanshi saboda ranar ne suka fara jin lafazin bakinshi.
Kallon da maina din yakewa suhail ya tabbatar tambaya ce cikin idanun nasa,amma yasan zaiyi wahala ya tambayeshin kai tsaye,don haka ya aza wayar saman qawataccen glass table din gabansa ya goye hannayensa a qirji yana duban idanun mainan
“Na fada soyayya da kallo daya tak aliyyu……I don’t know how to explain it….abun kamar shirin film,ganina daya tak da ita ta ban kuma ganinta ba,har yanzu ban mance fuskarta da kuma kamanninta ba…..ina jinta kusa da zuciyata qwarai,bazan kuma fasa nemanta ba a duk inda nake tunanin zan ganta”.
Kamar maina ya samu statue haka ya zuba masa idanunshi har ya kammala,suhail din ya fuskanci hakan,yasan halin mutumin qwarai da gaske,ba lallai ya fahimci dukka dogon bayanin nan nasa ba,don haka yaja dan qaramin tsaki yana daukar wayarsa
“Bansan me yasa na zauna naketa maka bayani ba bayan zuciyarka ba’a halicceta don taso diya mace har tayi sha’awar aure ba…….abu daya naga kana yiwa mahaukacin so wadannan yaran da bakasan nahiyar ma da suke ba” ya qarashe maganar yana zuba idanunsa kan wayarsa. Maganar tasa ta sanya maina maida dubansa saman fuskar tab dinsa,sannan ya zame tab din ya ajjiye yana hade hannayensa guri guda
“Me yasa ka yiwa zuciyata wannan fassarar?” Ya jefawa suhail tambayar da wani irin sound me taushi saidai kuma cikin tsakiyar taushin muryar tasa akwai wani irin deep amo me saurin isar da saqo kunnen me saurarensa koda baka shirya hakan ba.
Sai da suhail ya waiwayo ya kalleshi sannan yace
“Ah….. Mr man,nayi qarya ne?,ko iya yadda LAILAH keyi maka tsahon shekaru inajin ya kamata zuciyarka ta narke ka saurareta……amma fa banga alama ba,ba alamun zakayi giving up,ko kunyar sardauna baka ji?” Kai kawai ya kada yana kallon gefansa
“Akwai abubuwa da yawa da baki bazai iya bayaninsu ba suhail…….”
“I see” ya maida masa cikin gatse,sai kuma ya tsaya cak yana sake duban maina
“Kai…….if i can remember kamar naga face din yaran nan zuwa na umra last fa?” A nutse maina ya sake kallonsa ba tare da ya motsa ko yace komai ba,saidai cikin qasa da second biyu ya fahimci ba wasa bane irin na suhail,da gaske yake
“Really?” Ya tambayeshi yana dage dukka girarshi biyun
“Yes…..da gaske nake…..kaman a hannun rival dinnan da kaji ina bawa sardauna labari…..a harami ne tabbas” haka kawai ajiyar zuciyar da maina baisan dalilinta ba ta kufce masa,muryarsa so cool yace
“Zuciyata gaba daya ta karkata zuwa umra,ka dubamin yadda zan samu ticket da wuri mana please”
“Kai da ka fini xuwa akai akai ai kaman ka fini sanin masu siyan ticket da wuri ko?”
“Baya nan man din…..baya kusa” ya amsa mishi da alamun zaquwa sosai cikin muryarsa,sannan shigowar Moses wanda ya fito daga kitchen dauke da breakfast tray na ogan nashi yaja hanakalinsu.
Rusunawa yayi ya gaida suhail,suhail din ya amsa masa yana dan janshi da tsokana kadan sannan moses din ya wuce yana shirya dining
“Amma zuwa nayi muji yaushe sardauna zai dawo,mu kammala lissafi saboda nasan kowa yana da nashi plan din ko?”
“Bazan zauna jiran sardauna ba…….kuyi komai koda bananan ba matsala bane,tunda idan na dawo dinma duka duka bazan haura sati daya ba zan wuce paris……next month asibitin zai fara aiki in sha Allah”
“Alright……ba matsala” suhail ya fadi yana lalubar wata number
“Kwana nawa zakayi?” Idanunsa na a rufe,yatsansa guda daya ya dagawa suhail sannan labbansa suka motsa da
“Month”. Sai ya maida kansa ga dannar wayar,ya sani duk sanda maina ya shiga irin wannan mode din bai fiyason takura ko yawan magana ba,wannan ya sanya suke dauke masa qafa da kuma yi masa uzuri,duk da basusan taqamaimen damuwarsa ba har kwanan yau.
****Benazeer da batoul ke akan gaba janye da wasu kyawawan qananun qawatattun luggage dai dai su wanda ama ta bada order yinsu musamman saboda benazeer da batoul din tun daga dubai. Kowanne luggage na dauke da sunayensu a jiki da wani ruwan gold din rubutu. Abayar jikinsu ma haka ta kasance,gray color ce da tayi masifar dacewa da yanayin yaran. Kubul kubul dasu babu rama babu mummunar qiba,hutu jin dadi da zallar nutsuwa ta bayyana tattare dasu. Komai dake a jikin dayar akwai jikin dayar,abinda zai matuqar rudar dame kallonsu yayi tsammanin mutum daya ne aka tsagashi gida biyu,don hatta da rufaffen takalmin dake qafarsu na kamfanin D&G ba abinda ya banbantasu dana juna,haka siririn agogon gold dake hannuwansu.
Suna gaba ama da sultana na biye dasu,su dinma abayar ce a jikinsu me matuqar tsada da daukan hankula.
Batasan me ya sanya ba wannan karon tunda suka diro madeena gabbanta suke a sanyaye,tayita neman tsari daga sharrin shaidan koda shike da niyyar hanata ibada wannan karon tuquru kaman yadda ta saba,tunda shi din maqiyin duk wani dan adam ne,ta sanya hannunta ta gyara zaman glass dinta dake taimakawa ganinta,wanda akayi mata tun a wancan lokacin da idanunta suka samu raunin gani. Tun zuwansu Austria ama ta sanya aka sabunta mata shi,aka maidashi na ado sosai,a wancan lokacin qin yin amfani tayi dashi,sai a sannu data fara fahimtar inda rayuwarta ta sanya gaba ta nemeshi,ya zuwa yanzun kuwa tana nan dasu kala kala,dukkansu zaka dauka tana sakasu ne saboda ado.
Ba yadda aba baiyi da ita ya fiddata a duba idanun ayi mata aiki me kyau ba amma ta qiya,tsoro takeji qwarai,tana ganin idan aka tabata ana iya rasa idanun duka ma.
Kamar ko yaushe suna isa masauki tayi wanka taci abinci ta wuce masallaci,tayita zuba idanun ganinsu benazeer da batoul amma bata gansu ba,har ta kammala ta dawo bata gansu ba.
Samunsu tayi cikin dakin sun baje kayan ciye ciye sunata fama,benazeer tafi batoul bawa abun muhimmanci,ita batoul da alama ta gama ta koma kan waya.
Harara ta watsa musu dukkansu sai suka nutsu,bata ce musu komai ba har tashiga ta sake wanka ta fito,sai ta samu dakin wayam da alama sun gudu wajen ama,ta gyada kai tana jan qwafa ta koma saman gado ta nade ta fidda wayarta tana dan duba wasu abubuwa da suka shafi channel din da take sanya ran farawa aiki tare da dakon jiran shigowarsu. A qalla yanzun sun fara girma,shekara hudu cikin ta biyar ai sun san gabas sunsan yamma,ba zata barsu haka siddan su dinga zuwa waje me alfarma irin wannan ba tare da sunsan muhimmancinsa ba. Har ta gama jiran bacci ya saceta basu dawo ba,basu hadu ba sai data tashi sallar asuba,sai data kammala tata sallar sannan ta tashesu sukayi tasu,ta ritsasu tana tambayarsu me ya zaunar dasu jiya?.
Inda inda suka fara mata,daga qarshe batoul ta sanya kuka, benazeer ce me bada haquri,ta musu kashedi sosai,wanda tana tsaka da yin ama ta shigo.
Dariya ta dinga yi ciki ciki,ita tunda take bata taba ganin alaqar uwa da d'a irin ta sultana ba,gaba daya ta zame musu wata senior master bawai mummy ba. Da ama tabi ba'asi sultana ta gaya mata,sai ama taqi bin bayansu
“Eh da gaskiyar auntynmu,daga yau a dinga qoqarin zuwa masjid kunji ko?,amma kuma auty ayi mana afuwa,a dinga tafiya daga baya zamu taho tunda munsan wajen kuma bamu da nisa,munyi alqawarin ba zamu sake zama daki ba,idan kuma mukace mun gaji a barmu mu dawo daki mu huta” ama ta fada tana hada hannayenta waje guda. Murmushi ne ya subucewa sultana hadi da nauyin ama,saita kada kai kawai,ama dai ta samu ta kwashe ‘yan jikokinta suka fice hawaye shabe shabe.
Tun daga ranar kuwa basu saba alqawari ba,kamar wasu manyan 'yammata,koda ta tafi zasu biyo bayanta,saidai kuma sai sun gama qailularsu,siye siyen chocolate da fadace fadacensu na tsakanin sako da sako.
Satinsu guda kacal bibi itama ta iso,sukayi jiranta ta gama nata ibadar suka wuce makka.
makka
Al_ajyad street
SWISSOTEL HOTEL MAKKA
Kai tsaye motar kamfanin dake da alhakin tarbarsa ta wuce dashi swissotel,wanda kusan duk sanda ya shigo garin makka din bashi da hotel din da ya wuce wannan,hotel ne da yake jin dadin zama cikinsa sosai,saboda daga nan yana iya hangen haram tarwai,har wasu lokuta idan yayi tsaye daga bakin window din dakinsa yakan yi addu’o’i sosai kafin ya sake labule ya wuce.
VIp suite suka bashi saboda cancantarsa da cab din,aka tabbatar da shigar da jakarsa ciki,da kuma tambayar abinda yake da buqata suka gabatar masa sannan suka danqa masa dakin a hannunsa.
A nutse yake cire lallausar rigar saman kayan jikinsa,daya daga cikin shigar ‘yan qasar hindu,riga ce me wando da top dinta qarama me budadden gaba,wadda an saqata ne da yadin zaren vicuna mai matuqar daraja da tsada. Da baya ya zauna saman sofa din dake dakin yana lumshe idanunsa,kanshi yana kallon sama yana furzar da numfashi da kadan da kadan ta cikin bakinsa da wata iska me zafi.
Wata nutsuwa ke zagayashi,a duk sanda ya tsinci kansa cikin qasar sai ya dinga jin zuciya da qirjinsa wasai,saidai kuma hakan baya hanashi jin wani abu a jikinsa,irin jin da me nauyin laifi saman kansa yakanji a duk sanda ya gujewa laifinsa da ya aikata. Tsahon shekaru yana jin wannan abun a dukka wani motsi ko tattaki na rayuwarsa,ko sau daya koda na minti daya zuciya ruhi da kuma gangar jikinsa basu taba samun hutu ba game da hakan,a haka ya rayu…….darare da yawa bacci yana qauracewa idanunsa……lokutta da yawa yana sarayar da baccinsa ya zauna dangwargwar,sautukanta……furucinta da lafazzanta suna dawo masa sabbi fil cikin kansa….. zuciyarsa na tuhumarsa,tana sake maimaita tuhumrsa,me yasa?……don me ya gaza kai zuciyarsa nesa?,don me yasa ya kasa haquri ya dauke kai?,me yasa ta gaza cin albarkacin nafessa?,ya cika alqawari?,yayi abinda ya dace?,a yau inda nafessa zata dawo duniya zaya iya fuskantarta?. Bai sani ba shima…..baisan me yahau kansa ba,baisan me ya fusgeshi ba……kawai yaji har cikin ransa ya aikata,hakan kima shine dai dai…..shi zai sanyata nutsuwa,shi zai zama mafarin lanqwasuwarta da shigarta taitayinta. To ashe dukka yayi bahaguwar fahimta,ashe muqulli ya sanya zai kuma bude musu sabbin shafuka da qofofin qaddara masau tsauri da nisan zango irin wannan.
Sai daya samu nutsuwa gabbansa suka huta sannan ya bude idanun nasa yana duban agogon dake manne a bango, mintuna qalilan suka rage a tayar da sallar isha’i,kuma yana da matuqar muradin samun sallar cikin jam’i,kamar yadda duk tsanani ko wuya ko a ina yake baya barin jam’in kowacce sallah ya WUCESHI,musamman asuba da isha’i saboda falala dake cikinsu.
Kayan jikinsa ya fara ragewa,yana cirewar yana jin yadda wayarsa ke qugi. Baiyi koda attempting din tabata ba,saboda yaga wacece me kiran,yasan kuma ba Wanda ya shaida mata ya tabo nan din sai suhail,yanzun kuma ba lokacin wasa ko lokacin bata lokaci bane,duk da dama can ya bawa wajen muhimmanci me tarin yawa cikin rayuwarsa,da har baya iya daukan lokaci baizo ba,to amma yanzun buqatu gareshi masu nauyi,wani babban aiki ne a gabansa da yake da buqatar jajircewa yayi addu’a da kyau.
Cikin kayansa ya fidda bathrobe ya rataya sannan ya wuce toilet abinsa.
A gaggauce suka iso swissotel suka kuma gama komai suka karba maqullan dakuna guda biyu kamar yadda suka saba,daya na ama da aba,daya kuma nata da su benazeer da bibi,don haka classic room suka dauka me gadaje uku.
Suna shiga ta duba lokaci,sannan ta sake duba babban agogon nan dake garin makka. Lokacin isha’i ya kusa yi,don haka a gaggauce ta cire kayanta don watsa ruwa,tanason a qalla takai tsakiyar dare gaban ka’aba,akwai tarin buqatu da take dasu,ta kuma tabbatar tayi imani tare da yaqinin amsasu a wajen kamar yankan wuqa yake,ba wata addu’a da tayi bataga karbuwarta ba,a yanxun ma tazo da kukan yankewar igiyar aure da tayi saura tsakaninta da maina,don bata da qwarin gwiwar sake fuskantar su aba da zan can. Tun tana kasa kunnuwa taji aba din ya nemeta harta fidda rai,kullum zancan yana a ranta,saboda xuwa yanzun tasan girma da nauyin igiyar dake kanta tsahon shekarun……..
“Ku gama abinda kukeyi da wuri,da minti goma yau zan rigaku fita” ta fada tana daga musu yatsunta gami da shigewa toilet din,sai bibi ta bita da kallo tana kama baki,abun mamaki wai yau sultana ce da tsantseni da tsananta tarbiyya
“Yar nema,kina kamarsu ma sanda kike zuwa daki kike kwance abinki har muje mu dawo kina bacci shine yanzun da wanan sirisirin hannuwan naki kike irga musu lokaci” qaramar dariya ta saki tana tsaka da brush,don fes taji abinda bibin ta fada. Itakam ta karanceta irin mutanen dake son jikoki da yayan jikoki ne fiye ma da yadda sukewa yaransu da suka haifa soyayya
“Allah yabar mana ke bibi” ta fada qasa qasa tana tuna wasu lokuta na quruciyarta can shekarun baya murmushi ya sake subuce mata
“Ba abinda bashi da iyaka sai ikon Allah” ta fadi a ranta
KACIBUS……….😂INJI HAUSAWA DON BANA QARASA BA,SAI NACE KUZO MUJE 🏃🏽♀️🏃🏽♀️
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA.
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 45
Sun dudduba benazeer sun kuma tabbatar masa ba komai,don dama faduwar ba wata babbar faduwa bace. Dariya ta dinga yima maina
“Uncle……wai tsoro kaji?,banji ciwon komai bafa,faduwar ma kuma babu zafi” ta fadi tana dariya gami da tafa hannuwa. Idanunsa shidai carrr a kanta,sai ya saki qaramin murmushi sannan cikin tsokana yace
“Na ganki ‘yar lukuta ne,kuma lukutaye basu da qarfi,sannan ma ance mutum idan ya cika fari shima bashi da qwari wai” ya qarashe fadi yana dan tabe baki kaman zai saki kuka yadda yara qanana sukeyi. Wannan karon har batoul sai data qyalqyale da dariya,sai shima ya biye musu yana tayasu,suka amsa receipt suka fito daga pharmacy din.
Shagunan ice cream ya nufa dasu,yaja kujera kawai yayi zamanshi abunsa kamar wanda bashi da sauran aikin yi yace su duba duk wanda sukeso. Aifa benazeer an samu abunyi,duk bayan daqiqa sai ya waiwayo ta dubeshi
“Uncle a sakamin banana flavor?”
“Eh a saka miki” sai ya amsata yana murmushi,bayan wata daqiqar saita waiwayo tace
“Uncle vanilla fa?” Sai ya sake murmushi yace
” A baki” at last ya fahimci sun saba da shansa ne,kuma suna sonsa sosai don haka yace da ma’aikacin wajen
“A musu takeaway na dukka flavours din da suke dasu”. Murna ya kama benazeer harda qaramar rawa,shikam yana zaune tamkar wanda ya samu tv dake bashi nishadi.
Duk yadda suka sake dinnan dashi abinda ya bashi mamaki,qememe wani sukaqi bin wani balare da yace musu shagon gabansu zai siya musu gift na Pizza. Suka hau kallon kallo gami da maqale kafada suna kuma satan kallon maina din. Dariya suka bashi suka kuma burgeshi qwarai,dole sai nan ya siya ya kawo musu,a nan dinma maina ne yace su ansa,saboda yasan wajen wajene mai aminci,ba wani abu na cutarwa ko me cutarwa da zaiyi tasiri a wajen.
Shi ya riqo musu ledan suka qarasa haram sukayi sallah tare dasu bayan kowacce ta gyara mayafin abayarta,ya dinga dariya sanda suke gardama tsakanin benazeer da batoul,ita batoul tace lallai sai benazeer ta sauya alwala saboda ta fadi,kuma ma tayi surutu da yawa,itama kuma ta dage kai da fata alwalarta ba abinda tayi,da qyar ya raba gardamar.
Kiran wayarsa da akayi ya sanyashi miqewa don ya matsa gaba kadan ya amsa wayar saboda wajen da sukayi sallar yana ganin bai kyautu ya daga wajen ba. Yana Allah Allah yacemusu su tsaya ya maidasu masaukinsu amma number dake kiransa din tana da matuqar kima da martaba a wajensa,don haka ya taka a hankali yana qoqarin dagawa.
Kallon benazeer batoul tayi tana miqewa
“Mun dade B,nidai tafiya zanyi,kya taho”
“Bamu yiwa uncle sallama ba” ta fada cikin yanayin damuwa tana kallon hanyar da yabi
“Gobe sai muyi masa” ta bata amsa tana sanya takalmanta. Miqewa benazeer din tayi tana yarda da maganarta,suka gama sakawa suka dauki ledarsu sukayi hanyar da zata sadasu da swissotel hotel.
Sassanyan turarenta ta feshe jikinta dashi bayan ta kammala sanya rigar baccin me taushi da rashin nauyi,ta maida turaren ta ajjiye tana satar kallon bibi dake kwance tana kallon tv. Daga kai tayi sai suka hada ido da sultana
“Wai ina yarannan ne suka tsaya haka?” Bibi ta fadi tambayar kuma data yiwa sultana din dadi kenan. Abinda taketa lissafawa kenan cikin zuciyarta,sun dade fin yadda suka saba,duk da dama shiriritarsu yawa ne da ita amma basa kaiwa haka basu dawo ba.
“Ban sani ba bibi,hala shiriritarsu suka tsaya” ta amsa mata cikin basarwa tana ninke abayar data cire
“Ke kinga banson kidifirin banza….sanya jilbab dinki ki bisu,don kunga waje amintacce ne kunsan ba abinda zai faru dasu amma ai yana da kyau a dinga bibiyarsu ko?” Bata musa ba ta miqe ta saka hijab din nata,don dama abinda takeso tason yi kenan,kunya da kawaici ya hanata. Bata taba tsammanin akwai yaran cikun zuciyarta da rayuwarta gaba daya ba sai yanzu.
“B fuskar uncle fa kamar ba santa Allah” benazeer ta fadi tana yamutse fuska irin na yara masu surutu da shegen wayo. Harara batoul ta balla mata tana tura baki gaba
“A’ina kika sanshi,yau muka fara ganinsa fa,kuma Allah duk sai na gayawa auty da ama abinda kika dinga yi” ido ta zaro tana kallon batoul din
“Me kuma nayi?”
“Ba an hanaki surutu da kula wanda baki sani ba,shine kiketa bashi labarin school enmu ko da fada masa sunayenmu”
“Kuma daga wannan shine zakice zaki gayawa aunty?,don Allah B kinji kada ki fada,kinga uncle ai yana da mutunci,kuma ai don ya bugeni ne na kulashi,bazamu sake ma ganinsa ba inajin tunda bamusan ina yake ba”
“Sai an fada din” ta fada tana murguda baki tare da fitowa daga elevator din bayan ya tsaya a floor dinsu benazeer ta biyo bayanta tana magiya.
“Meye ake cewa kada a fada?” Suka tsinci muryar sultana dake qoqarin shiga elevator ta fasa saboda ganinsu.
Tsuru tsuru dukkansu sukayi,sai kuma suka hau kallon kallo. Idanunta ta zuba musu sosai yadda ta saba musu duk sanda takeson gano laifi ko gaskiyarsu,a hankali kuma ta maida dubanta ga ledar hannunsu
“Daga ina kuke?,waye ya baku wannan kuma?” Tayi furucin tana nuna ledar
“Uncle haidar ne” benazeer ta furta da shagwababbiyar muryar nan tasu data cakuda da sauti na tsoro.
“Uncle haidar?,waye haidar kuma.?” Ta tambayesu gabanta na wani irin faduwa,sunaye ukun nan a duniya,duk lokacin da zata jisu sai sun barwa zuciyarta razani ALIYYU HAIDAR MAINA.
“Mun taho masallaci na siya ice cream dina ya bugeni ya zube,shine ya kaini pharmacy aka dubani ya kuma siyo mana wannan” yadda suka tsorata ya sanya ta sassauto
“Da nace kada a siyoshi sai anyi sallah shine bakuji ba?,ku wuce ku bani waje” ta fadi a dan fadace. Da sauri sauri har suna rige rigen wuceta a tsakaninsu suka bar wajen,tana nan tsaye sai data tabbatar sun shiga dakin sannan murmushi ya qwace mata. Tabbas idan bakayi da gaske ba yaran saisu maidaka wani abun wasansu.
Kudin hannunta ta duba,akwai abinda takeson sauka qasa ta siya itama,don haka ta matsa gaban elevator din tana yunqurin kiranshi, saidai ta nuna mata akwai mutum ciki dake haurowa saman,wannan ya sanya ta tsaya daga gefe tana danna wayarta tana jiran isowarshi.
Kansa yana qasa,shima kuma wayar yake dannawa,a haka ya fito itama idanun nata nakan waya ta sanya kai ciki. Lokacin da suke gifta juna......iskar data debo kowa ta bugi dan uwansa har cikin jini da jijiyoyinsu sai da sukaji wani irin yanayi. Turarensa shi ya fara bugar da ita ya kuma haifar mata da qaqqarfar faduwar gaban data fusgi hankalinta,ta kuma kawar da hankalin nata daga kan waya,ta daga kanta tana duban bayansa......yana takawa ne a hankali kamar bayasin taka qasar,tsayyayen namiji me cikakkiyar siffa da zati,kwantacciyar sumarsa dinnan na kwance luf daga qeyarsa da take iya hangowa, dogayen hannayensa dake dauke da wasu veins kawai take iya hangowa,ta zubama bayan nashi idanu tana jin mahaukacin bugun da zuciyarta keyi irin wanda bata taba ji tayi irinsa ba,tilas ta yiwa kanta da kanta tambayar a fili yadda iya labbanta ne kawai suka motsa
“Waye wannan?” Ta furta idanunta bisa bayan nasa. Tayi imani ba’a banza zuciyarta ke wannan bugun ba,tayi yaqinin koma waye akwai wani abu me qarfi tsakaninsu,tabbas!!!!….. zuciyarta ba zatayi wannan bugun da ya sabawa qa’ida ba muddin ba wani abu mummuna ke shirin faruwa da ita ba,wanda wannan tunanin ya sake haukata bugun zuciyarta.
Shi kansa yasan ya danyi nisan tazarar taku tsakaninsa da elevator din yana replying saqon da ya zame masa kaman dole ne ya amsa din bawai don yana so ba…….amma cikin kowanne jini dake harbawa jikinsa wani abu yaji yana bibiye da harbawar tasa zuwa qwaqwalwa da zuciyarsa. Cikin jikinsa yaji kamar akwai wasu idanuwa masu kaifin gaske dake kallonsa,akwai wani dake bibiye dashi daga bayansa,wannan ya sanya ya juyo a hankali zuwa saitin elevator din,daidai sanda ta gaji da barin kanta da kanta a hangame ta soma rufe kanta.
Cikin idanuwanta idanunsa suka fada,haduwar idanuwa hudun da suka bada wani gigitaccen yanayi cikin zukata da qwaqwalensu. Dukkaninsu jinsu sukayi kamar daga wata duniya suka fado kwatsam ba tare da kowannensu ya shirya ba,babu wani dake iya cikakken motsi bare yunqurin janye idanunsa tsakanin shi da ita,har sai da qofar ta fara motsawa zata rufe din. Kamar wani magnet ya jashi haka yaji,ya fara takawa da wani irin sassarfa da hanzari yana nufar elevator din.
Ruf ta rufe kanta kafin yakai ga isa,yana miqa hannu kuma ta fara sauka qasa dauke da sultana wadda ta kama qarfen jikin elevator din kam ta riqe gudun kada takai ga faduwa,saidai kuma duk da hakan zuciyarta da ruhinta dukka sun gaza samar mata da qarfin da zaya iya riqeta a tsayen,dole ta sulale a hankali cikin elevator din ta zauna dirshan tana jin kamar tana shirin fita a hayyacinta ne.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 47
A nutse ya rufe mas hafin qur'anin dake hannunsa,yayi addu'o'i na wasu sakanni sannan ya maidashi ya ajiye. Wayarsa ya jawo ya bude,makeken hoton benazeer da batoul dake saman screen din wayarsa ya bayyana. Sunyi matuqar kyau cikin wasu pink gown,komai dake jikinsu pink ne,hatta ribbon da aka musu adon ka dashi da qananun dan kunnayen azurfa masu pink din duwatsu ne.
Ajiyar zuciya ya sauke karo na babu adadi,fuskoki ukun wunin yau duka su suka hanashi kuzari ko wani karsashi. Fuskokin yaran da baisan meye hadinsa dasu ba yakejinsu da wani irin qauna me zurfi a zuciyarsa,da kuma fuskar sultana.
Yes,sultana ce,ba wani abu ba kuma wasu shekaru yanayi ko zamani da zai iya hanashi ganeta,halittar daya raina da hannunsa ya bata dukkan kulawa. Ko ina yaronsa?,da waye yake kama?,ya girmansa yanzu?,duk bai sani ba,yana kuma daya daga cikin burikansa a yanzun. Yayi zirga zirga yau din tsakanin haram zuwa cikin hotel tsakanin kowacce sallah amma baiga wani abu da yayi kamanceceniya da ita ba. Ciwon kan da yake fama dashi duka yau bai barshi zama a masallacin ba,dole idan ya idar da sallah yake dawowa daki ya kwanta,amma yanzun da ake shirye shiryen kiran sallar isha'i sai yaji yana da muradin sake fitan. Yanason sake ganin yaran,ko suma sun nemeshi oho?,ko a wanne hotel suka sauka?,duka bai sani ba.
Alwala ya sake duk da wancan bai baci ba,ya feshe jikinsa da turarensa ya sanya qaramar hular da bahaushe ke kira tashi ka fiya naci saman kansa sai gashi ya fita a balarabe sak,ya sanya takalmansa ya fito a dakin.
Yana takawa har zuwa cikin haramin zuciyarsa na masa saqe saqe iri iri,bakinsa da kuma zuciyar tasa duka ambaton Allah sukeyi. Zuwa yanzu yanajin kamar ya rufe ido ya bude ya ganshi a nijer,yana jin ya shirya facing duk wani challenge.....duk wani tuhuma da kuma kowanne hawa da sauka bore da kuma bijirewa daga gurin koma waye.
Cikin tsantsan sawa kai nutsuwa da kushu'i akayi sallan isha'i da shi,ya kammala dukka addu'o'insa,sai ya samu kansa da zama a hanyar da sukayi clashing da yaran jiya,saman wata concrete chair.
Yana lazumi a hankali iskar wajen kuma tana ratsashi, cikin ruhinsa kuma yana jin kewar yaran,sai ya dinga hango fuskokinsu a jiya,daga shi har cikin yaran a cikin nishadi suke,dukka moment da sukayi spending tare ya zame masa memorable.
“Uncle haidar……. uncle haidar” ya jiyo muryar dab da shi. Kaf qasar a yanzun yasan su daya ne zasu kirashi da wannan sunan,don su kadai ya gayamawa wannan suna,a ko ina da aliyyu maina yake amfani,idan yaso ya qara da MAYAK’I.
Idanuwansa ya bude yana waiwayawa,dukkansu suna sanye da jilbab daidai jikinsu da yayi matuqar haskasu ya kuma qara musu kwarjini. Daga benazeer me giggiwa har batoul miskila murmushi sukeyi masa,alamun dake nuna sunji dadin ganinsa qwarai da gaske.
“U are highly welcome my BB” kafin ya gama kaiwa qarshen zancan ma benazeer ta zagayo tana neman gurin zama kusa dashi
“Dama na cewa batoul zamu iya ganinka fa,tunda aunty bata kiramu ba mu duba ko zamu ganka kafin lokacin komawa gida yayi” murmushi ya saki yana juyawa wajen batoul,yayi mata alama da hannu kan ta taho. Bata musa din ba ta zauna a daya gefan nasa,ya basu hannu sukayi musabaha dukkansu yana gaidasu da larabci. Ga mamakinsa sai yaji sun responding masa,yadan zaro idanu
“Wanne yare da wanne kukeji?” Dariya benazeer ta bushe dashi tana kallonsa,saita nuna masa yatsa hudu
“Ehnn……wanne da wanne?” Ya tambayeta irin amazingly dinnan yana fidda murmushi
“Hausa,english,arabic……. France small small” dariya sosai ta bashi da yadda ta fadi small small din tana daga qaramin yatsanta.
Kai ya jinjina sosai suna sake burgeshi,da alama sun samu background me kyau ta kowanne fanni na rayuwa
“Za’a yimin magana da kowanne?” Kai suka gyada kusan lokaci guda,sai ya saki murmushi yana gyara zamansa sosai a gaskiyarsu,yana jin zuciyarshi da ruhinsa yana masa wani irin dadi,yana jinsa tamkar a tsakiyar ahalinsa
“Bari na gayawa kowa abinda zaice” yana rufe baki benazeer ta maida masa da arabic,sannan ta sakeyi da sauri ta maida da France,sannan ta sake maida masa da english
“Daman da hausan ka fada” ta qarashe zancan da fadin hakan. Dariya ne ya kamashi,fararen haqoransa dake a jere ras suna sheqi suka bayyana.
“Na yarda….yanzun muje na bada gift na wannan abun” ya furta yana miqewa. Duk sai yaga basu motsa ba,ya waiwaya yana dubansu
“Oya…… muje”
“Aunty zatayi fada uncle” batoul ta fada tana maqale kafada. Dawowa yayi ya zauna ya dafa kansu
“Idan zatayi fada kuce uncle ne ya baku sabeel…..kun gane?”
“Idan mukace haka ba zatayi fada ba?” Kai ya gyada yana murmushi,duk sai suka sauka da karsashinsu suka bisa.
Kaman jiya ya musu siyayya,saidai yau din ya siya musu dai dai daidai yadda zasu iya cinyewa ma a gurin,gudun kada ya sanyawa iyayensu rashin nutsuwa a zuciyarsu da kuma ayar tambaya. Tsakiyarsun ya zauna sunata ciye ciyensu suna qananun fadansu da ba'a raba sako da sako,wani lokaci kuma su sakashi a ciki ya raba ko su jefashi a hirar su har suka gama.
Sanda ya niyyaci rakasu suka fidda idanu,suna tsoron ya hadu da sultana,don ko jiyan susan banda sun iso da wuri data fito nemansun nan saita gansu,sun tabbatar kuma zasusha fada qila harda punishment
“Uncle zamu iya zuwa da kanmu” idanunsa ya lumshe yana gyada kansa
“Goodnight”
“Goodnight uncle” suka maida masa,zukatansu dukkansu cike da shauqi,kowanne a cikinsu yana jin kamar kada ya rabu da dan uwansa.
Sai daya qara wasu awanni a wajen,ya sake addu'a sosai yana neman ubangiji ya shiga lamarinsa. Sai kusan sanda dare ya raba sannan ya wuce masaukinsa.
A dakin kusan abun jiya ya hanashi bacci. Fuskar sultana da a yau yayi mararin su sake ganin juna,da kuma yaran. Baisan wacce jarrabawa ce take bibiyarsa akan yaran ba,amma yana jin wata irin tsaftatacciya kuma tatacciyar qaunarsu cikin zuciya da ruhinsa.
***Dukka kwanakin da suka rage musu cikin makka din a darare take,kowanne motsi sai take ganin kamar zata ganshi a masaukinsu kowanne fita da yaran zasuyi sai taji kaman zasu hadu,kaman zai kwashe yaran a nemesu a rasa,kowanne fita tata cikin kaffa kaffa takeyi da lura da duk inda zata gifta din. Tun daga rabar bata sake bin elevator ba ta gwammace tayita bin stairs har takai qasa,wanda idan ta fita din sai tayi zamanta cikin masallaci,idan ta dawo ciki kuma ta dawo din kenan sai kuma washegari. Duk sanda tayi hanyar elevator sai taga kamar zasu sake haduwa,kaman zata sake ganinsa irin yadda ta ganshi rannan.
Kwana hudu kacal da suka rage subar makka su wuce nijer sukayi wani irin sabo dashi,hakanan shima yayi wani sabo dasu ta yadda har bai tuna haduwa sukayi kuma kowanne lokaci shi ko kuma su wani zai iya tafiya yabar wani. A jikinsa yake jin kamar gurin zamansu daya,kamar wani family ne shi dasu dake rayuwa cikin gida daya,kamar a nan zasu dawwama da yaran. A kullum bayan sallar isha'i sai ya zauna ya jirayesu. Duk irin yadda yake girmama lokaci......duk irin yadda ya tsani jira cikin rayuwarsa,duk kamewa irin tasa da rashin shiga sharafin kowa.......duk uban miskilanci da tsananin ginshira irin nashi amma bayan sallar isha'i saiya bata wananna awa daya zuwa biyun. Ko yana zama su iso,ko yazo ya samesu zaune a wajen suma suna jiransa. Ice cream da chocolate sun sha har babu iyaka,masu tsada ya koma siya musu irin wanda canjin da ama ke sanya musu cikin jaka bazai isa su siya ba,babu kuma me biyewa ciye ciyensu a cikinsu bare ya bisu ya siya musu da nasa kudin,don dukkansu sunsan girman wajen,zaman masallacin yafi komai cinye lokacinsu a wuni guda.
Tunda benazeer ta fahimci a ranar zuwa azahar jirginsu zai bar makka hankalinta ya soma dagawa,tasan dai ba zasu kai lokacin da suka saba haduwa da uncle ba bare suyi sallama,ta kuma gaya masa zasu tafin. Gaba daya sai ta kasa sukuni,tana cikin kujera a kwance tana ta kallon batoul dake cin chips da fork,tana ta son ta kalleta suyi shawarar yadda zasu ga uncle su gaya masa zasu tafi,shima yaushe zai tafi?,yaushe kuma zasu sake ganinsa?.
Yawan surutu kuzari da karsashin batoul ya sanya kusan kowa ma ya fahimci tana da damuwa. Tuni sultana ta fahimta,amma saboda kawaici da batason fiya zaqewa cikin lamuran yaran bayan ga qashin bayansu nan jigonsu a gurin saita kauda kai,saidai kuma tanata monitoring komai nata,ta kuma karanci tsaf akwai abinda yake damunta ya kuma hana mata sukuni.
Qaramar akwatinsu da ama ta shirya musu tsaraba a ciki tazo ta ajjiye,saita juya kadan tana kallon benazeer
“B….me yake damunki yau?” Tayi tambayar cikin salon nuna muhimmancin tambayar saman fuskarta. Zamewa tayi ya sakeyin lamo cikin kujera,sannan ta motsa qaramin bakinta
“Ba komai”
” Da gaske?” Kai ta gyada a hankali
“Ko kuma kayan shaye shayen sanyin nasu takeso ba,tunda na fahimci duk sun zama shazumamu,sunma fi uwarsu son shan jarabbaben zaqin nan ai” Dariya ama ta danyi,ta jawo purse dinta data shigo da ita ta fidda riyals tana cewa
“Su kenan suka ragemin dama……aje a siyo na bankwana” ta furta tana murmushi. Idanu sultana ta dauke gefe zuciyarta na motsawa,zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba ganin soyayya tsakanin kaka da jikokinta ba irin ta ama da su batoul. Haqiqa bibi ta sota,ta qaunaceta,ta kuma nuna mata soyayya me yawan gaske…..amma akwai wasu kusakurai da ramuka masu yawa a hanyar,wadanda tasan ta tsallakesu ne kawai saboda qilan taci albarkaci ko darajar wani ne.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA.
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 48
Da sauri benazeer ta miqawa ama qaramin hijabinta ama din ta sanya mata, batoul ma ta ajjiye abincin tana sanya lausasan wasu rufaffun takalma masu kyau suka sanya kai suna ficewa riqe da hannun juna,ama ta bisu da
“Ayi addu’a”
“In sha Allah” suka hada baki wajen fada.
Sai da benazeer ta tabbatar sun sauka sannan ta kalli batoul
“Nifa uncle zan nemo na gaya masa mun tafi fa” ido batoul ta zaro tana kallonta
“A ina zaki ganshi?”
“A inda muke zama,muje mu siya ice cream sai mu dawo mu wuce ta wajen ko zamu ganshi” dan jim tayi kaman me nazari,sai kuma tayi murmushi
“Muje to”.
Shop din da ya saba kaisu suka shiga,suka zabi kowa flavor din da yakeso,har ma'aikatan wajen suna tsokanarsu
“Yau babu fada?,ina uncle din nasu?” Dariya sukayi, benazeer tace
“Baizo ba?,nemansa muke” daya balaraben yace
” Tare kuke zuwa, sai dare yake zuwa tare daku” basu wani fahimta ba,sundai gane kawai baizo ba don haka suka sanya kansu suka fice benazeer na cewa
“Ma’assalama”. Suna riqe da ice cream din suna sha suna kuma bin duk hanyar da suke ganin zasu iya ganin uncle haidar amma babu shi babu dalilinshi,har batoul ta gaji,taja tunga sanda aka soma kiran sallar azahar
“Kizo mu tafi gida tunda bamu ganshi ba,kada aunty tayi mana fada,ama ma kuma tace fa mu dawo da wuri” juya idanuwa benazeer tayi kaman me shirin sakin kuka,ta sake waiwayawa bayanta kamar me fatan ta bude idanunta ta ganshi a wajen,saita dawo da kallonta ga batoul wadda itama dinma duk ranta ba dadi
“Muje” ta fadi a sanyaye. Haka suka jera suna komawa hotel din ba um ba um um. Sanda suka isa dakin duk sun fice zuwa sallar azahar,amma kuma kayansun sun gama hadasu tsaf,kowacce saita samu waje tayi lamo ba wani me magana ko kuzari a cikinsu.
Koda suna shirin fita a dakunan saida ama tayi qorafi
“Anya lafiya kuke kuwa.yau dinnan?” Ta fadi tana taba wuyansu,sanyi taji ba alamun zazzabi ba komai,batoul ce tace mata ba komai
“To Allah yasa alkhairi” aman ta furta,saboda tsahon tarenta da yaran bata taba ganin jikinsu ya mutu haka ba.
Nannauyan numfashi ta sauke tana furzar da iska daga bakinta. Cikin ruhinta takejin wani salama da nutsuwa suna saukar mata,zuciyarta kuma tana gaya mata tayi masa nesa ta tsere masa. Ta window din take kallon fadin sararin airport din,tana jin kewar barin qasar kamar yadda ta saba,amma tana jin farinciki idan ta tuna ta tserema idanun maina,sannan nan gaba kadan zata dawo ta sake ziyartar dakin Allah.
Tafiya miqaqqiya daga birnin makka har zuwa qasar nijer. Tafiyan awanni goma sha daya suka sauka a niamy,daga nan wani jirgin suka sake hawa suka wuce marad'i.
Iska ta shaqa sosai ta qasar nijer sanda tayi relax cikin daya daga cikin lafiyayyun motocin mallakin aba da ama. Wasu emotions suna cakuduwa cikin zuciyarta,qamshin qasartata yana motsata tare da tuna mata abubuwa masu yawa,wanda kusan fiye da rabinsu quruciyarta ne......yarinta da zallar wauta da ta tafka a rayuwarta,wani abun ya sanyata murmushi wani ya bata takaicin da shima din dai murmushi ne na dole ke qwace mata.
Tun barinta nijer zuwanta daya kacal......wannan shine zuwa na biyu da tayi,zuwan daya banbanta da zuwanta na farko. A yanzun ta sake dawowa qasarta a matsayin cikakkiyar sultana,me yara har guda biyu,wadda ta mallakin hankalin kanta......sannan masaniya cikakken sani a harkar ilimin jarida. Sultanar da a yanzun kai tsaye zaka iya kiranta da madam. Dukkan wata sura da halitta nata na kyawu ya gama cika,ya kuma cakuda da zallar kwarjini da hasken ilimi. Ta zama classy qwarai,ta banbanta da girman tazara da wancan sultanar me rawan kai yawan surutu fitsara da rashin kunya. Yanzun ta zama wata sultana me yawan shuru shuru,wadda ba shirgin kowa take shiga ba,abinda ya shafeta ma ba kowanne take daga idanu ta kalla ba har ta bashi lokutanta.
Isowarsu qofar makeken gate din mansion house din mallakin MAYAK'I ya sanyata daga tsintsiyar hannunta tana gyara zaman siririn agogon gold din dake hannunta,lokaci ta duba murmushi ya subuce mata sanda hancin motarsu ke shiga harabar gidan. Ba wani abu ta tuna ba illa lokaci irin wannan da take hada dabar hira,sam qawaye mata a sannan ba damuwarta bane,maza ma sunfi mata dadin qawance qwarai,saboda su din zata musu tsiwa tayi musu fitsara kuma su daga mata qafa don suna kallon ita macace kamar sauran mata. Idanunta cikin farfajiyar gidan da ta sake qawatuwa qwarai,anyi mata gyara sosai,da alama kuma dukkan gyaran yana da nasaba da bikinsu aminata ne. Ko ina yayi fes,tamkar sabon gini,tamkar ba wannan tsohon ginin da qarfi d kuma qoqarin NADEEYA ya samar dashi shekarun baya ba. Ko kusa ko alama mamallakan gidan basu taba barin tsufa ko shekaru su cimmasa,saboda kusan koda yaushe cikin aikin gyaransa suke,duk wanda ya samu dama a cikin kawunnan nata saidai kawai mutanen gidan suji ana shelar a kwashe ko za'a yi aiki.
Idanunta ta janye sanda suka sauka a wannan bigiren....muhalli ne da kusan yafi zama a cikinsa akan ko ina cikin gidan,waje ne da yake zama yana kula da shige ficensu yana kuma monitoring motsinsu da tarbiyyarsu. A duk sanda zata kalli wajen koda sau dubu ne sai taji ranta ya baci sau dubun,shi ya sanya zabinta daya kauda kai a irin wannan lokacin.
Motarsu na tsaiwa kusan duk wanda ke wajen ya ankara da isowarsu. Kafin kace meye wannan mutanen dake cikin gida ma sun fara fitowa tarbarsu. Kusan kowa ya fito ta batoul da benazeer yake. Batoul sarkin rashin yarda da shegen miskilanci da taga ama ta kutsa kai cikin jama'a sai ta koma jikin sultana ta lafe. Abun sai ya soma baiwa sultana kunya,saboda idanuwa data ja mata,kowa sai ya matso ya tsokaneta ya kuma tsokani sultanar,wadda a sannan idan kaga batoul dake jikinta zatayi rantsuwa yayarsu ce bawai uwa mahaifiya ba. Ko kusa ko alama duk qwaqwafinka baka isa kaga alamun sultana ta isa ta mallaki tiqa tiqan yara har guda biyu kamar benazeer da batoul ba.
Wata motar ce ta shigo,najma aminata da yasmine ne a ciki amare. Najma ke driving aminata da yasmine da houda cousin dinsu suna baya,a kujerar gaba kuma djamilla ce itama dukka kakanni daya suke dasu sultana.
A gaggauce najma ta tsaida motar,dukkansu cike da farinciki suke qoqarin fitowa,saidai ta rigasu ma qarasowa,fuskarta dauke da nutsatsen murmushin nan nata,da muryartannan me sanyi tace
“An fara yawon amarcinne?,amma ko a jirani?” Junansu suka kalla da dan mamaki,ba wanda ya kawo zata nema sakewa a cikinsu shi yasa wasu abubuwan ma basu tsara da sunanta ba
“Zaki iya yawo a cikinmu?” Houda ta fadi tana ‘yar qaramar dariya. Waiwayowa tayi tana dunan houda da murmushin da ya tsaya saman kumatunta tace
“pourquoi pas?(me zai hana?)” Ta fadi tana kallon houda
“Yar jarida ce ke yanzun a qasar France…… kinga dole muyi takatsantsan karmu shiga ajin da ba namu ba” dole ta sanya sultana sakin siririyar dariya,siraran jerarrun haqoranta suna bayyana
“Banason sharri houda…..har yanzun baki sauya hali ba?”
“Inaaaa……wannan canjin saiku……na rantse bada wasa ba ko…….ban ganeki ba sai da kika matso sosai” kada kai tayi tana murmushi,tasan halin houda da kyau,tun suna qanana,tasu tafi zuwa daya saboda halin tsokana irin nata na da da take dashi
“Amma sœurs(yan uwana)su ba zasu kasa ganeni ba ai”
“Nima canzawarki ta jawo”
“Ku bani hanya naje naga babies dina,don idan aka biye taku naga alama zamu jima tsaye a nan” aminata ta fada tana maida headphone dinta qaramar handbag din dake hannunta. Rufe qofofin motar sukayi suka fara takawa gaba dayansu zuwa cikin gidan,suna tafe suna tattaunawa akan dame dame aka tsara yi a bikin.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FA
MILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 49
Sake duba agogon wayarsa yayi don bai fito da agogo ba. Wannan dubawar yana irge ita ta zame masa cimakin dubawa na goma sha biyar kenan. Zubawa fuskar wayar idanu yayi wadda ke dauke da hotunan yaran,yaja godon numfashi daya sauka har cikin huhunsa. Kanshi ya sake dagawa yana duban jama'ar dake shige da fice cikin haram din wai ko zai ga gilmawarsu,saidai ko twins guda daya bai gani ba bare ya sanya ran dasu a ciki.
Ya fara sarewa da ganinsu yau,saboda tun wancan ranar da suka hadu din basu taba kaiwa warhaka basu iso wajen ba,basu taba latti kaman haka ba,kamar yadda basu bata fashin zuwa ba.
Dauke kansa yayi ya maida idanun nasa qasa,sai ya samu kanshi ya tsawaita a addu'a cikin zuciyarsa na zuwan yaran a nan kurkusa. Bayajin zai samu nutsuwa ko qanqani idan bai gansu din ba,zuciyarsa da rayuwarsa a kwanakin jinsu yakeyi a rikice gaba daya,hatta da suhail da sardauna da basu kusa dashi suna iya fahimtar haka cikin mu'amalarsu dashi.
Duk wata tattaunawa da ya shirya zasuyita through video call ya kasa halarta,wani lokacin ma sai sunyi sun gama zaiga miscal nasu. Idan sun matsa da yabi sai yace musu duk yadda suka yanke yayi. Duk kawaici na sardauna sai daya magantu
“Kafi kowa sani daddy bazai amince da dukka abinda zamuje masa dashi ba saiya tabbatar bisa yarda da sahalewarka ne tunda dai kaine jagora……kuma ma,ta yaya zaka jagoranci harkar lafiya a qasar dake da tsari da doka kana cikin dimuwa haka? what’s wrong with you ne maina?” Sumarshi kawai yakan shafa duk sanda suka masa tambaya irin wannan,don baisan amsar da zaya basu wadda zasu fahimceshi su kuma gamsu ba,abu daya ya sani,Allah yana sonshi da ya kawo masa irin wannan yanayin a wajen da dukkan dimautacciyar zuciya ke samun nutsuwa,a muhallin da amsa addu’a bashi da shamaki da ubangijin dake amsa roqon bayi,banda hakan shi kansa baisan a wanne yanayi zaya kasance ba.
Miqewa yayi bayan ya fahimci ya sake qara wasu mintuna ashirin din masu kyau,ya zube hannayensa a aljihun kaftan abaya dinsa ruwan bula(navy blue)wadda ta sake fidda ainihin kyawunsa na cikakken ba'abzine kuma bafulatanin buzu,sai ya tsinci kansa da gangarawa bangaren shops din dake hada hadar saida ice cream da sauran kayan zaqi,wajen da yasan duk dare shi dasu suna zuwa.
Kai kawo ya dinga yi yana duba ice cream din zuwa chocolates din,saidai kawai yana zaba ne shi kansa baisan me zaiyi dasu ba. Nan dinma ya kashe kusan awa guda amma baiga alamarsu ba,har yakai lokacin da.ya tabbatar a irinsa ne suke ce masa sun tafi,daha qarshe ya fidda riyals ya biya uban chocolate da ice cream din da ya zaba yace su kyautar wa duk yaran da suka shigo.
Cikin wani irin nauyin jiki da na zuciya yake komawa swissotel, zuciyarsa a mugun quntace da wani irin rashin dadi,duka ya rasa target dinsa,ba sultana ba kuma yaran,sai ya dinga jin kamar lokaci yayi shima da zai bar wajen,lokaci yayi da zai cimma sultana,cikin nijer......cikin gidansu.
Yana fitowa daga elevator wayarsa ta dauki tsuwwa,sanda ya fiddata yaga me kiran sai da yaji kamar ya kyautar da wayar,don baya cikin mode na amsa kowanne kira. To amma hausawa sukace wata fuskar tafi gaban mari,ko don sardauna kawai kafin akai kan daddy,dole ta sanya ya daga kiran ya kara a kunne.
A yangance tayi masa sallama,da qyar ya hada kalmomin amsa sallamar tata,yana jin kamar numfashinsa baya sauka cikin hunhunsa da kyau
“Am sorry,zan kiraki wani lokaci” dan jim tayi,kamar bataji dadin furucin nasa ba,amma kuma sai tace masa
“Okay” a taqaice sannan suka ajjiye wayar kusan a tare.
Kasa haquri yayi,kafin ya isa daki ya lalubi suhail. Komawa yayi ya jingina da qofar dakin bayan ya maida ya kulle,idanunsa a kulle,kunnuwansa na sauraron yadda kiran ks gangarawa wayar suhail,gefe daya kuma yana sauraron bugun zuciyarsa.
Sama sama suka gaisa,kai tsaye ba kwana kwana ya gabatar masa da uzurinsa
“Banason na wuce kwanaki biyar suhail ban isa nijer ba”
“Why?,me yasa kake caccanzawa kamar wani wahainiya ne maina?”
“je ne sais pas non plus(nima ban sani ba)”ya fadi da harshen faransanci
“Me kace?” Suhail din da yaren turanci yafi yawa cikin nasa harshen ya tambayi maina abinda yace din
“I don’t know suhail…… I don’t know why”
“But amma kasan a yadda muka tsara zakayi koda one week ne a Paris a gama komai koda a tsaitsaye ne sai ka wuce”
“Noooo suhail,no…..bazan iya ba,koma meye ya jiraci dawowata……na gaya maka…..kwana biyar kadai zan qara a nan din…..bazan canza ba” daga haka ya katse wayar don kada ma suhail din ya sake kawo masa wani hanzarin,don bayajin akwai wani abu a yanzun da zai iya dakatar dashi kai kanshi nijer din.
*Tunda suka sauka a nijer shirye shiryen biki kawai ake cikin gidan babu kama hannaun yaro. Da fari ta soma halinnata na dararewa da kebe kanta akan komai,daga bisani su aminata suka mata bore kan basu yarsa ba
“Abinda yayiki shi ya yimu,kuma meye hujja ki dalilinki na tsame kanki daga cikinmu sultana?,bayan idan kin koma paris sai mun ganki fa” wannan dalilin ya sanya tayi qoqarin sakewa sosai a cikinsu. Duk wata hidima sai sun tsomata a ciki. A hankali saita fara warewa,wannan yanayin……wannnan yanayin……wannan lokacin da wancan zamanin dukka da ya dade da shudewa cikin rayuwa da mafarkanta sai ya dinga farfadowa. A hankali ta dinga samun nishadi cikin zuciyarta,wani nauyi dake qirjinta ya dinga raguwa kadan kadan. Son kadaicewa……jin kanta kamar ta banbanta dasu ya dinga raguwa sosai.
Mutum daya ke neman matsanta mata,babu daman ya gansu sun fito sai ya matso gaban motarsu,idan anci sa'a ita keda driving ranar kafin ya iso take maka baqin glasses wa idonta ta finciki motar su fice,najma tayita mitan ta bari mana ko wajenta zayazo amma bata bi kanta,idan kuwa najma cw driver dinsu na ranar to ya samu yadda yakeso. A fakaice yake gasa mata maganar
“Karki manta,tu es la femme de quelqu’un d’autre(ke matar wani ce)” Baisan iya adadin yadda kalmar ke motsa zuciyarta ba,sai ranar da abun ya qureta kawai taji hawaye ya tsinke mata. Cikin arashi kuwa a gaban idanun uncle bashar abbanshi,shi yayi masa tas yace su shige mota su tafi abinsu,Allah ya tsare. Daga ranar ta samu sauqinsa,saidai fa hausawa sunce me hali baya fasa halinsa,duk ko yaya ya samu dama sai ya sake fesa mata,duk hade ranta da dauke kanta bai dameshi ba.
Siyayya sosai ama tayi musu na biki a dan tsakanin,kayan gargajiya na hausa sosai,ready made na atamfa da laces,don su benazeer din basu da wani kayan gargajiya sosai saboda yanayin inda suka taso. Kafin wani lokaci ama ta kammala musu komai,don wasu abubuwan amma matar uncle bashar ta kammale musu dama.
****Tun yammaci ta sanya driver ya dawo da ita gida ta baro su aminata suka wuce wajen booking musu lallen biki. Ba yadda batayi su cire sunanta ba amma najma tace
“Sai kiyita yi” najma ta fadi tana jan motar, driver modu ya jata ya dawo gida da ita.
Duka saurin da takeyi don ta amsarwa ama girkin aba. Tana sallar la'asar ta kammala komai,qarfe biyar aba ya aiko atta a fito musu da girkin wani kebataccen waje daga bayan gidan,da alama suna sa tattaunawa ne shi da uncle omar da oncle bashar.
Tun daga nesa ta fahimci zaman na musamman ne,akwai invitation na daurin aure da yawa a wajen da sauran takardu.
A nutse ta durqusa ta ajjiye musu komai akan tsari,sannu dukka suke mata. Iya 'yan kwanakin kawai kowanne mamakin sultanan yake,kamar ba sultanar data fita a gidan bace wata ce daban aka sauyota.
“Allah yayi albarka,ya shirya miki zuri’arki” aba ya fadi cikin qauna da kuma tausayi
“Ameen aba” ta amsa ranta yana mata fari sosai
“Bashar……ka rubuta cikin calendrier (schedule) na abinda zamu tattauna…..mu duba yadda zamu warewa marainiyar Allahn nan igiyar wannan yaron daga kanta don mu bata damar rayuwa cikin ‘yanci kamar kowacce yarinya…”.
Wani numfashi ta zuqa me zurfi da nauyi tana jin kowanne gaba ta jikinta na rawa, zuciyarta ta motsa sosai da wani irin matsanancin bugu,qafafunta na hardewa ta qara sauri tana barin wajen ba tare da ta jiyo amsar dasu oncle bashar suka bawa aba ba……
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 50
Da dan sassarfa ta qarasa sassan bibi don shi yafi qarancin mutane. Dakin bibin ta wuce don rabonta da dakinta har ta manta,tun wancan ranar sam bata iya shiga dakin ta zauna,saidai idan wani abu zata dauka kota ajiye,tana shiga kuma take fitowa.
Sai datakai can quryar gadon sannan ta kwanta,rigingine tayi tana qoqarin ganin fitar numfashinta ya dai daita. Tsahon wasu mintuna sannan ta motsa bakinta a Hankali idanunta na runtse
“Ya Allah…..ya rabbussamawati ka bawa wannan bawan naka ikon rabani da wannan alaqaqai din igiyar” tayi addu’a tana fita daga tsakiyar zuciyarta.
Har cikin ranta taji addu'ar ta karbu da gaske,sai taji tadan samu nutsuwa,ta juya barin hannun damanta tana fadada tunaninta na yadda zata tafi da rayuwarta cikin 'yanci,tana sake fadada mafarkinta na zama fitacciyar 'yar jarida a duniya. Da wannan tunanin a hankali a hankali bacci yazo yayi awon gaba da ita.
Washegari me qunshi ta musamman dakewa ama qunshi tazo yi mata. Su benazeer tace a fara yiwa. Da farko batoul taqi yarda wai tsoron lallen takeji,tunda ba'a taba yi musu ba tunda sukazo duniya. Bibi kaman ta ari baki,ta dinga fada
“Haihuwar faransa rainon faransa…..ai dole,ba abinda kuka sani daya shafi al’adar africa…..don lalacewa atamfa nan murna wai yarannan suke zasu daura zani,laifin hamdiyya ne…….banga ta barinku ku tabbata a turai ba,gwara ku dawo nan kusan rayuwa” Dariya surukai da sauran ‘yan uwa dai daiku da suke wajen suka dinga yi. Benazeer babu tsoro ita ta fara miqa hannunta akayi mata,sai da batoul taga benazeer din ta cire,lallen yayi matuqar kyau a fara tas din fatarta, benazeer din nata murna tana shafawa,abun yana bata sha’awa ita karan kanta sannan batoul ta yarda ayi mata.
Matsawa batoul din tayi kusa da sultana dake shirya duka kayan da zasu sanya cikin bikin a wasu madaidaitan akwatuna guda biyu,ta zura mata hannun saitin fuskarta
“Auty bakiga hannuna ba?,kaman ba nawa ba auty,kema ayi miki,zaiyi miki kyau aunty” tayi nisa a tunanin da ita kanta batasan na meye ba,haka kawai tun jiya gabanta ke yawaita faduwa,ta laluba kafff batasan dalili ba,saidai zuciyarta tafi raja’a akan kodai tana tunani akan wanne hukunci su aba suka yanke game da makomar igiyar auren dake kanta?,tayi winning ko batayi ba?.
Fararen idanunta masu yalwataccen gashi ta daga ta kalli fuskar yarinyar,sannan ta maida ga hannun da taketa zura mata. Ita kanta hannun yarinyar ya burgeta,jan lallen ya kwanta saman jar fatarta kamar jan lalle saman hannun balarabiya
“Ma sha Allah,tabarakar rahman……kinyi kyau sosai” farinciki sosai ya kamata,ta buga tsalle saman katifa tana kiran yaran da suke gurin sa’anni kamarta tana gaya musu
“Kunji ko?,ko aunty ma tace nayi kyau”.
Washegari wuni sur basu zauna ba suna wajen lalle,qin yarda tayi ayi mata daga farko don batason me yawa,tafiso sai an yiwa kowa me lallen ta gaji sannan ayi mata. Dan kadan din akayi mata,janne itama har bayan hannu sai na cikin tafin hannu,na qafa ma duka kadan akayi mata,ikon Allah sai ta zamana kamae zabarta me lallen tayi,gashi dai yafi na kowa qaranci amma kuma yafi na kowa yin kyau,ai kuwa suka yiwa me lalle caaa,itadai dariya ta dinga yi matar tana cewa
“Ba daga ni bane,daga me hannun ne……ina cewa kuna gani dai,fatarta tafi ta kowa kyau da haske” maganar matar dole ya sanya sultana murmusawa duk da jikinta da takeji wani iri babu dadi.
Ranar laraba aka fara biki sosai,komai nasu bisa tsari da kuma tarbiyya suka shiryashi,ba wani abu da ya wucewa tsari.
Duk wata shiga idan sultana din tayi sai ta fita daban,kallo kam ta shasu,ta tabbatar banda tana da yawan azkar tsaf baki zai kamata,komai nata me aji sanyi ds kuma nutsuwa. Wadanda suka jima basu ganta ba kuwa mamaki kowa yakeyi
“Wai wannan sultana ce da gaske?,wadannan diyoyinta ne?” Abinda kusan dukka suke tambaya kenan,wasu riqe da baki wasu kima fuskokinsu cike fal da mamaki. Itakam saidai tayi dariya ta wuce. Benazeer abun nema ya samu,ba zama wai an saci dan barawo,idan ta fice cikin jama’a sau tari sai ama tasa an nemota,bata nan bata can,kusan ita din akafi sani akan batoul,saboda kwata kwata ita din bame hayaniya da surutu bane. Duk da kamannin da suke dashi yana rikita mutane,amma kuma dabi’unsu ya sanya ake saurin banbancesu. Yawan qawayen da benazeer din tayi cikin dangi sai abun ya baka dariya ds mamaki,duk wani team na yara idan kaga sun hadu sai kaga itace shugaba. Sak SULTANA saidai wasi banbance banbance a tsakaninsu. Benazeer ta samu kulawar ama qwarai,data fuskanci yanayin dabi’u da halayenta sai take tarbiyyantar da ita daidai da halin nata,wannan ya sanya duk surutu da rawan kanta take da matuqar ladabi,tana da kirki tana da kyauta tana kuma da tausayi,bata iya rashin kunya ba sam, kusan duk wanda zata gaisar sai takai har qasa,saidai fa za’a cikaka da surutu da kuma labari. Randa aka soma bikin goumar baya nan,sai dare ya dawo washegari kuwa me daure musu qarqashi ya dawo?,ai har batoul itama saita bazama,basa zama sam,wani lokaci ma sai sunyi bacci da dare za’a shigowa ama dasu,sai kuma wata safiyar idan rai ya kaimu. Duk inda za’a suna gaban motar goumar din,kowa yasan nan ne mazauninsu ma bame zama wajen,haka aka dinga gudanar da event din daya bayan daya,komai ya qawatar ya kuma bada sha’awa.
Ranar juma'a itace ranar dinner. Qawatacciyar dinner da aka shiryata ga dukkan amaren da danginsu dana angwayen aminata da yasmine,ga dangin uwayensu mata,wannan ya sanya aka kama babban waje da zai dauki kowa da kowa a sake kuma akan tsari.
Tun asubar juma'a din ta tashi da wani dan qaramin zazzabi,har cikin qashinta take jinsa,hakanan kanta bangare daya yana sara mata lokaci lokaci. Idanunta ta lumshe tana mamakin abinda ya saukar mata da wannan zazzabin hade da bacin rai. Tasan dai lafiya lau ta kwanta bayan sun dawo daga kamun amare da akayi alhamis,sannan ba wani zirga zirga tayi ba,don ama ta bata daya daga cikin motocinta tace tayi hidimarta da ita,ko a canma tana zaune waje daya,saboda yadda idanu ke mata yawa suna binta da kallo duk inda ta motsa ne bata so,abinda kuma ya sake bata mata rai ta samu waje ta zauna,daya daga cikin abokan ango da tazo wucewa ta gefansu zata bude motarta ta daukowa wasu friends din su aminata sevenniours. Ya jima yana binta da kallo duk inda ta gifta,shine mutumin da ya sanyata ta dinga zabga tsaki har babu adadi,a yanzun kuma da zata wuce ta shiyyarsu sai yace da ita murya can qasa
“quelle douce odeur(qamshi me dadi)” har cikin ranta maganar da ya fada din taji ta soketa. Eh tabbas,ita kanta ta sani,tana amfani da wani irin mayen turare ne me masifar kama jiki da sanyin qamshi,qamshin da hatta su aminata sai da suka magantu akai,tana maitar son turaren wannan ya sanya ya gama kama jikinta,amma aiba huruminsa bane yayi magana akai ko?. Bata kulashi ba ko waiwayo batayi ba ta wuce abinta,saboda kulawa ma ai yabawa ne. Sanda ta sake dawowa bai haqura ba sai daya sake magana
“Banyi mamaki ba don baki tanka ba…..ko makaho kukayi gaba da gaba dashi zaisan ke ta musamman ce……tu es une femme chic(macace ke me aji)” juyawa tayi tana dubansa,kamar zata tanka saita tuna hala dama tankawar nata yake da buqata,don haka saita sake masa wani siririn tsaki ta wuce abinta,abun haushin sai ta jishi cikin murmushi yana cewa
“Merci bébé(na gode baby)” maganar data qular da ita kenan ta samu guri tayi zamanta.
K'ofar aka taba alamun knocking,daga jin knocking din tasan bazai wuce benazeer ko batoul ba,sassanyan muryar nan tata can qasa tace
“Entrez(shigo)” batoul ce sanye da wasu cotton sleeping dress. Tabi yarinyar da kallo,kullum da kalan kayan baccin da zata gani jikin yaran,itadai batasan adadin guda nawa suke dashi ba,ita kanta wasu abunuwan nasu batasan adadinsu ba,saboda ko yaushe ama cikin kashe musu kudi take,cikin musu siyaya take,bata kuma iya musu siyayyan abu me araha ba,komai sai ta zuba me daraja da tsada. Kullum sake girma sukeyi suna wani wayau,halittar da Allah ya musu kyautarta na sake bayyana,yadda taji ana zancan har kamar ma sunason juyewa kamanninta.
“tante……ki fito inji ama kiyi breakfast,taji kaman su Yasmin suna cewa zaku fita” idanu tadan fidda tana dubanta
“Yau kuma na koma tante,aunty din in English bai isa ba?” Dariya ta saki sosai irin me cike da quruciyar nan
“Tante yafi dadi aunty……duka su aminata haka ake kiransu,kema a nan sunanki tante,saimun koma nigeria ko Paris zaki koma autyn” kai kawai sultana din ta gyada,ta fuskanci yau da surutu itama BATOUL ta tashi,don tanajin tanja tanata fama dasu daga cikin kitchen
“Ganinan zuwa”
“d’accord” ta amsa mata da farshen faransanci tana ficewa a dakin da dan tsallenta. Janye idanunta sultana tayi daga qofar tana jin wani yanayi yana shigarta,haka kawai takejin tausayin yaran yana shiga zuciyarta,dukka tayi qoqarin danne wannan,ta jawo qafafunta ta sauka ta wuce bandaki.
Wanka ta sakeyi hade da brush don ta hada gumi saboda maganin saukar da zazzabin da tasha,kuma alhamdulillah sai taji ya sauka din,saidai kuma rashin qwarin jiki. Simple gown ta saka na wata cotton atamfa maras nauyi,don ita ta tsammaci ma material ne da farko da ama tasa aka dinka musu,ta lullube kanta da dankwali sannan ta dauki wayarta ta fito.
Fuskarta tayi fayau,ba komai saman fuskar sai dan alamun rashin jin dadin jiki. Akwai baqi a falon,ta bisu ta gaidasu har qasa cikin girmamawa. Wannan dabi'ar tabi jikinta durqusawa yayin gaida manya,tana daya daga cikin dabi'un da aka horesu dashi a hassan gwarzo. A nutse har ta qarasa dining,ta taras da houda salamatu dukka cousins dinta ne,suka gaisa ta samu kujera ta zauna tana duba abinda zata iya ci.
Tana ci suna hira a haka aminata ta fara shigowa
“Kun gama shiryawa?” Houda ta fara amsawa
“Mayafi na kawai zan dauko,Je pense salamatu est prêt(ins tunanin salamatu ma ta shirya)” ta fadi tana duban salma din,kai ta gyada alamun hakanne,aminata ta dubi sultana cikin kokwanto
“Kefa?” Dan motsawa kadan tayi sannan tace
“Ina ji fa sai dare zamu hadu gurin dinner din kawai”
“Baki isa ba” aminta ta fada tafa hannuwa cikin bala’i. Cikin sa’a yasmine ta shigo dai dai lokacin,suka hadu duka dinga mata. Ba wanda ta tankawa,don maganarsu ma so take ta daga mata ciwon kanta,ta barsu sukayi iya yinsu,amma yadda suka tarar mata tasan bata da mafita,salin alin ta koma daki ta dauko mayafinta kayan da zatayi amfani dasu da key din motar ta fito suka wuce. Mutun bibbiyu sukayi, yasmine da salma a motar salma din,sultana da aminata a motar sultana.
Katafaren beauty lounge ne da yayi suna cikin marad’i da kewayenta. Wajene da idan kinsan baki isa bama baki kai kanki wajen,service sukeyi na manyan mata tamkar a cikin gidanki. Tarba za’a miki da drinks lemo harda kalan abincin da kike buqata,itakam sultana dukka batabi takan wannan ba,sai ta wuce qurya salle de repos(resting room) nasu dake dauke da manyan sofas masu taushi tayi kwanciyarta. Tana jiyo duk wani karakainar su tana kuma hango motsinsu ta cikin babban glass da ya rabasu.
Idonta ta lumshe haka kawai yau takejin ta rasa gane kanta da kanta,hannunta ta zura cikin jaka cikin sa’a taci karo da tasbaharta,saita maqalata a yatsa ta soma hailala don mugun faduwar da gabanta keyi yana bata tsoro.
Awa biyu tsakani taji ta kasa nutsuwa,saita dauki wayarta ta soma kiran tanja. Har ta katse bata daga ba,da alama bata kusa,kasa jurewa tayi ta sake kiranta,bugu biyu ta dauka. Hayaniya ya fara cika kunnenta kafin muryar tanja
“Benazeer da batoul fa?” Ts tambayi tanja kai tsaye,tambayar data bata dan mamaki,shigen tambayar data taba ma ama a makka,amma saita share mamakin tace
“Suna lafiya…..suna tare da goumar”
“Yayi……shikenan” ta fadi tana katse wayar,ajeta tayi saman kanta tana furzar da numfashi,duk sanda akace mata suna tare da goumar nutsuwar zuciya da ruhi take samu,duk da irin yadda shi goumar din baya gajiya da cakar da ita da kuma tsokanarta,tasan wannan a jininsa yake,kuma akanta kawai cikin yaran gidan yake haka,duk da ita ta fara sanadin sanya masa sunan BAQIN BUZU da tayi.
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 51
Kaman kowanne event sai sun tsokaneta bayan kowa ya gama shiryawa,yanzunma sun buwayeta da ya akayi komai lite tayi amma yafi na kowa kintsuwa da yin kyau. Ta gaji da wannan zolayar tasi,ciwon kai kawai sukeson qara mata,don haka ta fita daga wajen ta koma mota ta zauna tana jiran isowar angwayen da zasu dauki amarensu su wuce gurin dinner gaba daya. Har a lokacin jinta kawai takeyi sama sama,basu jima ba kaman sunsan a qage take suka iso,dukka motocin suka tashi a tare suka wuce.
MAINA
A nutse nutsuwar dake bayyana a iya fuska takunsa da ayyukansa na zahiri kadai.....yake saukowa daga matakalar jirgin da yayi jigilarsu daga niamy zuwa nan marad'i bayan dogon zaman da yayi daga makka a jirgin Ethiopian airlines.
Dogon ba'abzinen,Giant me wani irin qawataccen tsaho da murjajjen jiki......fari tas ma'aboci sassalkar cikakkiyar sumar da kai tsaye za'a kirata da sumar gado,sanye cikin wata farar shadda qal.....da aka zamanantar da dinkinta ya zauna a jikinsa tamkar don saboda shi shi kadai aka qirqiri dinkin. Dogon wando ne da gajeriyar riga ta ciki me gajeran hannu,saidai kuma an qawata shigar tasa da babbar riga da kuma dakakkiyar hular da bata rufa dukkan asirin sassalkar sumarsa ba. Daga nesa idan ka hangi tsahonsa da yanayin jikin gami da shigar tasa zaka dauka jinin hambararren shugaban qasar nijer ne wato mohamed bazoum,saidai kana kallon fuskar zata tabbatar wannan jinin MAYAK'I da jajirtacciyar tsohuwar yar kasuwa NADEEYA ne.
Gujajjen D'a daga ainihin qasarsa ta haihuwa,daga ainihin gidansu abun alfaharinsu,daga ainihin garinsa ahalinsa da kowa nasa......yau gashi cikin qasar da ya barta ba tare da sanin zuwa wanne lokaci zai dawo ba?,yau gashi kan hanyar komawarsa gidan daya fita cikin fitar hayyaci da rashin sanin abinda zai biyo baya,yau gashi zai fuskanci ABA AMA BIBI DA D'ANSA DAMA MAHAIFIYAR YARON SULTANA.
“Bienvenue Monsieur” yaji an fadi daga gefanshi da harshen faransanci ana yunqurin karbar luggage dinsa da suhail ne ya samu nutsuwar hada masa kayan nasa. Kai kawai ya gyada ya sakar masan,don already yasan waye,uniform din jikinsa ya sake gaya masa waye din,kuma aikin sardauna ne duka ya sani.
Yana biye dashi har suka isa gaban wata Mercedes Benz baqa wul dake daukan idanu qirar wannan shekarar ce da suka siyeta su ukun,shi sardauna da kuma suhail. Kai tsaye yace a turo tasa nan,a ajjiye a kamfaninsu dake shirin fara aiki a qasar tasu.
Yau ya fara ganin motar ido da ido,amma a yanzun bashi da cikakkiyar nutsuwar qare mata kallo,don haka shigewa kawai yayi back seat din da ya bude masa,ya maida motar ya rufe,ya shiga mazaunin driver ya tayar da motar suka dauki hanyar fita daga airport din.
Baisan wanne yanayi zuciyarsa take ciki ba,baisan kuma meye yakeji a dukka jikinsa ba,abu daya tak ya sani,zai fuskanci babban QALUBALE......zai gamu da komai,zai ga komai zai kuma ji komai,amma koma meye ya dawo da dukka qarfinsa,ya kuma dawo da shirin fuskantar KOMAI DA KOWA.
Unguwar tasu ya dinga bi da kallo,a tsahon shekarun akwai ci gaba sosai,komai ya sauya,ba wani abu da yaga yaci baya,har zuwa LOKACIN da ya driver din ya iso dab da gidansu.
Lumsassun idanunsa ya ware,ya miqa hannu ya taba kafadar driver din,da muryarsa dake can qasa yace
“arrêt(tsaya)” bai musa ba ya gangara gefe saboda ya bawa motoci biyun da suka biyo bayansa damar wucewa,ya tsaida motar daga gefe daya.
“Bani maqullin,tu peux y aller(zaka iya tafiya)”
“d’accord Monsieur(to yallabai)” ya fadi cikin girmamawa yana bude murfin ya fita kaman yadda ya buqata.
A hankali ya fito daga bayan yana komawa seat din driver idanunsa bisa babban gate din mansion house din nasu,jikinsa yana bashi wani hidima akeyi cikin gidan don yaga alamun haka,zuciyarsa ta raya masa wani abu da tilas ya rufe idanunsa yana kiran sunan Allah sannan ya tayar da motar
“Bana fatan na mutu ban gurfana gaban aba da ama ba……bana fatan na mutu da hakkinsu” ya furta a fili saidai can qasa bayan zuciyarsa ta raya masa kodai wani daga cikinsu ne ya rasu.
Motoci biyun da suka wuce su yabi,dukkansu security suka budawa hanya suka wuce ciki,saidai kuma ana zuwa kanshi suka jaa qofan saboda kasancewar motar baquwa a idanunsu,sannan kuma basu tabbatar da motar waye ba,don haka ba zasu bata daman shiga ba har sai sunyi checking nata.
Cikin dakewa da sanin makamar aiki daya daga cikin security din ke matsowa,idanu maina ya zuba masa,houdu ne,daya daga cikin security na gidan tun kafin barinsa gidan. Ya tabbatar shine mutum na farko da zaya fara shaidashi,saboda yasan fuskar tasa tun babu saje babu gemu,ya sanshi tun a sanda saje ne kawai dashi,a yanzun da gashi ke kwance luf bisa tsari na samuwar shekaru a tattare dashi bazai gaza shaidashi ba.
Abu daya tak yayi,houdu na matsowa yana sake glass din motar,dai dai sanda ya iso dai dai sanda shima ya kammala saukewar,sai sukayi ido hudu da MAINA din.
Duk wani connection na jikinsa ya katse cak na wasu mintuna,sannan second kadai ya dawo bisa saitinsa,idanunsa fes cikin nashi,sai yasa hannu yana cire hulan kanshi,sai maina ya dora hannunsa saman lips nashi dole houdu ya maida maganarsa cikin cikinsa,ya kuma juya ciki da sassarfa yana bawa saura umarnin su bude,ba musu tunda shine shugaba suka bude din ba tare da sanin waye cikin motar ba,ya dage glass dinsa ya danna hancin motar zuwa farfajiyar gidan bangaren ajiyar motoci bayan shekaru biyar da barinsa gidan...........
WELCOME BACK MAINA😂😂😂
Sanda take wucewa falon aba dauke da saqon aba a hannunta kunnuwanta sukaji qarar shigowar wata motar. A ranta take dariyar mugunta,tana kyautata zaton goumar ne ya nemo najma data boye ya maidota gida,don ta barshi a can ranshi bace yana nemanta,yayi rantsuwa bazai barta a wajen ba. Ta rasa wanne irin kishi gareshi haka?,abun goumar yana daure mata kai,duk da migraine da take fama dashi amma itama sai data rama yau dubu cikin abinda yake mata
“Ta can baya na ganta da wani farin buzu me irin tamu fatar” tayi furucin ko a jikinta tana bude motar ta cilla kayanta ta shiga tabar wajen tana hangensa ta madubi. Gun data fada din yakeson zuwa,amma ya dake yaqi nufar wajen yana tsoron ko tsiyarta ne yasa ta gaya masa hakan saboda yasan hali sarai,barin hali kuma sai mutuwa,ta kuma karanceshin itama haka ta dinga dariya cikin mota ita kadai har ta fice a wajen.
Daga qafarta zata sanya a falon aba din yayi daidai da qarasa shigowar motar gidan,ba kasafai hankalinta ke kaiwa ga shigowar motoci gidan ba,amma wannan sai taji gabanta ya yanke ya fadi. Dan dafa saitin qirjinta kadan tayi tana cewa
“Hasbiyallahu lailah illa huwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem”
“Waye a nan?” Muryar aba daga cikin falon ya isketa daga nan inda take
“Aba nice,saqon oncle sidi ne” ta amsashi tana qarasa shigowa ciki. Sai data shigo din taga bashi daya bane,kamar kusan kowacce rana,tunda aka fara hidimar bikin basa rabo da irin wannan zaman waje daya. Oncle bashar oncle umar da oncle issoufou,sai qani ga mahaifinsu da bai jima da dawowa nijer ba.
Bakinsa dauke da sunayen Allah ya ajjiye motar kan tsari kaman sauran motocin gidan,ya kasheta ya kuma zura qafafunsa yana furta
“Bismillah” ya taka dandagaryar qasan gidan. Sai daya kulleta sannan ya juyo,juyawar daya samu security na gidan tsaitsaye daga bayanshi suna kallonsa cikin tsantsar mamaki. Murmushi ya jefesu dashi,sannan ya juya yana fuskantar ainihin ginin gidan,zuciyarsa na shawarta masa INA YA DACE YA FARA NUFA?. sassa guda biyar din dukka sai sukayi masa kwarjini,daga qarshe zuciyarsa tayi masa ragama izuwa sassan AMA saboda tuna masa da tayi UWA CE,zata iya zame masa tsanin zuwan kowanne qalubale da sauqi.
Kasancewar kusan kowa bai dawo daga wajen dinner din ba sai daidaiku,sai ya dinga tafiyarsa ba tare da yaci karo da kowa ba. Daf da qofar sassan ama din yaja burki kaman yadda wanda ya fito da hanzari dauke da gorar babban lemo a hannunsa shima ya tsaya cak kamar an tsaida mashi.
Almu ne,wani irin kallon gigita da bazata yake bin maina dashi,sai gorar lemon hannun nasa ta sulale ta fadi qasa. A nutse maina din ya duqa ya dauko masa,ya bude tafukan hannayensa ya zura masa a ciki ya kuma damqe hannun cikin nasa,sannan cikin karyayyar muryarsa yace masa
“Kaini wajen ama” maganar tasa saita zamewa almu kamar wahayi,bai musa ba don dama tun dacan ba musu tsakaninsu,bai kuma iya tambayarsa komai ba saboda tsananin mamaki ya wuce gaba maina yana biye dashi.
Yasan inda ya baro ama din yanzun daya fito daga wajenta,tana falon farko wanda take da bedroom a wajen,ya barta suna hada shimfidun da za'a fitarma dakin baqi na gidan ita da tanja,don haka suna zuwa dai dai qofar dakin yaja ya tsaya yana bawa maina hanya,tamkar yana nufin
“Ya maina na gama nawa” idanun almu din ya kalla,sai ya sake kama hannunsa ya riqe sosai
“Ka jirani koda a nan ne,kada kaje ko ina” kamar mataccen qadangare almu dai ya gyada kai,yayin da maina ya sanya hannu ya murza handle din dakin ya sanya kai bakinsa dauke da cikakkiyar sallama……..
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 52
Sallamar tasa ta iske kunnuwansu dai dai sanda ama ta miqawa tanja blanket din tana cewa
“Kowanne gado a canza don Allah kafin mutane sukai ga dawowa daga wajen dinne………” Cak sauran maganar ta tsaye mata a qasan maqoshinta,kowanne gaba na jikinta yayi wani irin mutuwa gami da yin sanyi kamar anabi ana zare mata laka.
Sake maimaita sallamar tasa yayi cikin karyewar murya da zuciya gaba daya,wata irin qaqqarfan qaunar mahaifiya tarin madama da jin cewa shi cikakken me laifi ne yana taso masa. Gabanta na faduwa ta kalli tanja,tun bata yiwa tanjar tambayar ba tasan amsar tambayar tata,amma saboda tabbatarwa sai tace mata
“Tanja?,muryar waye kunnuwa na sukeji?” Ta furta da wani irin sauti muryarta da mugun sanyi
“Shine….” Tanja ta fadi itama kamar me tsoron gayawa ama din. Wata qatuwar ajiyar zuciya ce ta kufcewa ama din,ta runtse idanunta sannan ta budesu,taja numfashi sosai cikin hunhunta sannna ta fesar,sai ta durqusa tadauki wani madaidaicin blanket din ta sake miqawa tanja tana ci gaba da yi mata bayani tamkar ba wata halitta baquwa data wanzu a wajen
“Ki ajjiyewa su bilkisu saiki dawo,akwai ragowar aiki a nan din” taci gaba da bayaninta.
Iya yadda tayi wannan motsin ya tabbatarwa maina akwai qototuwar matsala,ya taka zuwa bayanta jiki a mutuqar sanyaye,ya sulale a hankali ya zube bisa gwiwoyinsa kanshi a qasa ya kasa furta komai.
Cikin jikin nata taji alamun yana bayan nata,sannan satar kallon bayan nata da tanja takeyi yasa ta sake fahimtar a bayannata yake tsaye har yanzun. Wani nannauyan abu yana fusgar zuciyarta,dukka zuciyarta da kwanyarta na shirin shiga rudani,bataso ta waiwaya ta kalleshi......bataso ya saukar mata da rauni a a matsayinta na uwa,idan tayi rantsuwa ko kaffara ba zatayi ba tasan cewa kaf gidan gurinta ya fara dosowa kanshi tsaye.......ta tabbata ba wanda yasan da shigowarsa cikin gidan sai ita,akanme zata sassauta masa?,akan me zata bari zuciyarta tayi rauni cikin lokaci qalilan har haka?,tsugunnonsa da zamansa ba zata tana bari suyi mata tasiri ta kasa aiwatar da abinda ya kamata ace ta aiwatar din ba.
Dukka kayan tanja ta dauka sannan ta soma takawa tana barin dakin,duk taku daya sai ta waiwaya ta kalli maina har ta fice,yayin da ama kuma ta soma hada wasu kayan,duk da batasan ainihin me zatayi da kayan ba ita kanta. Cikin jikinta takejin wani irin yanayi,karyewar zuciya da mutuwar kowanne sashe na jikinta,yadda yanayin bugun zuciyarta ya sauya ta tabbatar akwai fushi me tsanani kwance a qasanta
“Assalamu alaikum…….don Allah ama koda ba zaki kulani ba ki amsa koda sallamata,ki amsa min da neman aminci da albarkar ubangiji da na rasa tsahon shekaru” maganar tasa sai ta zame mata kamar famin wani tsohon miki dake danqare qasan zuciyarta. Watsar da kayan hannun nata tayi sannan ta gewayeshi da hanzari zata fita a dakin.
Cikin wani irin zafi irin na namiji yasha gabanta,sai ya sake zubewa a gabanta yana riqe da dukka qafafunta da hannayensa
“Don Allah ama……na roqeki……ko sallamata kawai ama ki amsa min” janye qafafunta baya tayi da sauri,karon farko ta watsawa fuskarsa wani irin kallo …….wani rauni ya sake mamayarta. Mainan ta ne……ya zama cikakken mutum……mainanta ne…..ya zama babban mutum…..aliyyu ne da ya bar gabansu tsahon shekaru,yanzu gashi duqe gabanta cikin qoshin lafiya da dukkan alamu na nutsuwa da kwanciyar hankali tattare dashi
“Waye kai?,nace kai din waye?,don kaga na qyaleka a matsayinka na bare ka shigo har cikin dakina shine zaka zaqe da yawa haka?” Ta jefa masa tambayar da murya me cike da fushi. Sosai kalaman nata suka daki zuciyarta,suka kuma so tarwatsata zuwa piece’s. Yau din shi ama ke barrantawa daga gareta?,shi ta maida bare?,wanda bata masan fuskarsa ba?. Ya hadiye wani qatoton abu daya tsaya masa a wuya,muddin ama tace zata qalubalanceshi ta haka bayajin zai iya dauka,ya shirya fuskantar kowanne irin fada da ladabtarwa,koda kuwa suka ne,amma bazai iya jurar shariyarsu da wofantar dashi haka ba.
“Danki ne ama,ba wani bane daban,aliyyu ne ama……maina ne……danki bijirarre gujajje…..me tarin laifuka a gareku…….don martabar manzon Allah S A W ama kada kice ta wannan hanyar zaki horani” girman roqon da yayi mata yayi matuqar tasirin wajen rauna mata zuciya,amma hakan bai sanya ta kasa sake janyewa baya ba ta kuma nufi qofa da sauri tana jin kamar hawayen da take riqewa zasu balle kansu da kansu saboda girma da nauyin dake danqare cikin qirjinta…….ta jima da sarewa…..ta dade da fidda rai daga samun rayuwarsa,tana raye ne kawai tabarwa kanta abinda zuciya ke yawan raya mata a kanshi…..amma sam bata taba hasashen rayuwar aliyyu na nan tabbace saman doron qasa ba.
“Indai kazo ne na goya maka baya……na tayaka binne laifinka ba zaka samu haka ba aliyyu……nice mutum ta qarshe da zaka fuskanta,hukunci na shine hukuncinna qarshe da zaka karbanan din ba shine mihallin da zaka fara fuskanta ba” abinda ta gaya masa kenan a gaggauce ta fice a dakin,wani irin abu yana zagayawa cikin jini da zuciyarta,tunaninta yana rarrabuwa. Tasan tabbas!,Allah ne ya amsa addu’arta……amma me dawowarsa ke nufi?,meye kuma zai faru a nan gaba?,wannan dukka bata da masaniya. Taja numfashi da kyau ta kuma fiddoshi waje,ga mamakinta sai taji dunqulallen abunnan daya tsaye mata a maqoshi tsahon shekaru……wanda ta gaza gane meye shi tsahon wancan lokacin yana narkewa a hankali yana sauka.
A lokacin yana jin dukka jikinsa ya masa nauyi,yana jin kamar bazai iya motsawa daga wajen ba......yana jin kamar kwanyarsa ta daina tunani dai dai,saidai kuma a hankali ya kama sunan Allah,ya fusgeshi da matuqar qarfi
“Alhayyu alqayyumu” ya fara maimaitawa,a hankali sai dukka qwarin gwiwarsa yaji yana dawowa,ya kuma sake kiran
“Allah!” Da qarfin zuciya yana miqewa,ya nufi qofar dakin ya bude ya fice.
Inda ya tsayar da almu a nan ya sameshi,suna hada ido almu din ya sunkuyar da kai
“Ina zan samu su aba?” Da hannu almu ya masa nuni da hanya tamkar wani kurma,maina din ya karanci me yake nufi,sai shima ya masa nuni da hannu akan suje din,almu yayi gaba,shi kuma yaci gaba da bibiyar sahun almu din dake masa jagora zuwa falon.
Gaban aba ta qarasa ta durqusa kamar kullum tana musu barka da warhaka. Dukkansu suka amsa cikin kulawa,ta sanya hannu ta dauki ledar tana miqawa aba fuskarta fadade da murmushi
“yauwa ma sha Allah,ya cika alqawari,ungo wannan” aba ya fadi sanda yake warware kilishin da sultana ta kawo masa. Murmushi tayi ta sanya hannu biyu ta karba tana cewa
“To na gode aba sosai”
“Madalla” ya amsa mata,sannan ta yunqura tana miqewa
“Kinga sultana…….ki shiga ki gayawa mariya su duba abinda yayi ragowa a kayan amfanin gobe” oncle umar ya fada
“To uncle” ta amsashi tana nufar qofar tana ji aba yana tsokanarsu kan cewa boye kilishinsa zaiyi,diyarsa kadai zai iya bawa. Murmushi ta saki qasan zuciyarta,ba abinda zata ce ma Allah sai godiya,itakam batasan maraicin uwa da uba ba.
Tsam almu ya tsaya daga bakin qofa ba tare da maina ya buqaci hakan ba, cikin jikinsa yaji bazai iya jerawa da maina ba,yana jin bazai iya jure hukuncin kallo kadai da maina zai iya fara maraba dashi daga dukka iyayen nasu ba. Bai waiwaya ya kalli almu ba,kaman ma baisan almun ya tsaya ba ya doshi babbar qofar falon. Ya tube tsadajjen sau cikin qafarsa,ya sanya qafafunsa dake saye da safa cikin falon yana janye labulen gefe bakinsa kuma dauke da cikakkiyar sallamar
“Assalamualaikum warahmatullah”. Wani dogon numfashi almu ya saki yana qamewa jikin bango gami da runtse idanunsa. Ya rantse da Allah…..tabbas inda shine ya maina bazai iya sanya kansa ga falon nan ba,ya rantse da Allah bazai iya fuskantarsu ba saidai idan tara tara za’a yi masa,wanne irin qarfin zuciya dakiya da jarumta ke gareshi?,ko kuwa dai baisan girman laifinsa bane a garesu?.
“Wa’alaikumussalam warahmatullah” sukayi hadin bakin amsawa,saidai kuma ba dukkansu bane suka samu cikakkiyar lada da daman amsa sallamar…….kamar yankewa zubar ruwan sama sauran amsa sallama ta tsaya saman harshen aba……yayin da oncle umar shima sauran furucin suka tsaye masa cak. Wani irin rawa zuciyar aba tayi bayan daukewar sallamar daga bakinsa,a nutse kuma sai ya dauke kansa daga kallon qofar falon ya maida ga takardar kilishinsa ya soma qoqarin nannadeshi.
Cikin qasa da second biyu da shigowarsa dakin da fitar sallamar daga bakinsa idanunsu suka gauraya waje daya. Haduwar idanun data zame musu wani abu na bazata dukkaninsu. Batayi zaton ganinsa ba.....baiyi tsammanin samunta a wajen ba......hasashe ko tunaninta bai kawo.mata ganinsa a nan kurkusa ba. Wani wawan birki taja a matuqar Hautsine,a hankali taji hankalinta yana neman firgita,nutsuwarta na shirin yin qaura daga ganganr jikinta. Wannan haduwar dai dai take da MUGUN GANI a wajenta...... mummunar rana da kuma mummunan lokaci......maina cikin gidan?,a wannan daren?,a kuma irin wannan lokacin?. Tambayoyin da suka kusan tsayar mata da gudun numfashi tsakanin qirjinta da zuciyarta zuwa hunhunta kenan.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
BOOK 02 PAGE 53
Dukkan zagayayyun lion eyes dinnan nasa ya kafeta dashi. Karon farko......lokaci na farko da sukayi gaba da gaba dashi. Karon farko yau gashi tsaye a gabanta,a gaban wata sultanar da ko kusa ko alama baiga tayi masa kama da wancan sultanar da ya bari shekaru biyar baya ba. Wani irin qaton abu yake ji yana gangarowa daga zuciyarsa me matuqar nauyi yana kwaranyewa zuwa sassan jikinsa.
Da wani zazzafan karsashi ta janye idanuwanta,wata irin wuta na ruruwa cikin qahon zuciyarta. Har tsakiyar qirjinta takejin wani irin zafi yana sauka,ta soma takawa cikin bawa kai qwarin gwiwa ta kewayeshi tana nufin fita daga dakin, zuciyarta na jaddada mata bata da hadi dashi,ruhinta na gaya mata cewa bata sanshi ba......bata ma taba saninsa a rayuwarta ba,tana kuma sake bawa kanta yaqinin bata da wata alaqa dashi.
Dukkan kowanne sashe na zuciyarsa muradin binta da kallo yakeyi,abinda ya gani qasa da second goma cikin qwayar idanunsa ya matuqar razanashi,to amma sanin da yayi cewa abinda ke gabansa da kuma mutanen dake zaune cikin falon din dai dai yake da tunkarowar yaqi cikin rayuwarsa sai ya tattara dukka wani abu daya taso ya tsaye masa a wuya yayi musu muguwar hadiya,hadiyewar daya haifar da ciwo a qirjinsa da kuma jirkicewar ainihin launin qwayar idanunsa.
Tamkar gagarumin me laifin dake takawa zuwa gaban alqalin da zai yanke masa hukuncin mutuwa ko rayuwa haka yaci gaba da daga qafafunsa da kuma saukesu yana tunkarar mutanen da ya tabbatar suke da matsayar ci gaba da fuskantar rayuwarsa a yanayin daya kamata ko akasin haka. Dukkaninsu idan ka dauke mutum daya tal wato ABA idanunsu yana kanshi,kowa yana dubansa ne da zallar tarin mamaki da kuma bazatar bayyanarsa a irin wannan lokacin.
Dai dai sanda ya zube a tsakaninsu aba ya miqe,ko sau daya ko alama bai nuna yasan da shigowarsa ko wanzuwarsa cikin dakin ba
“Issoufou idan kun gama ka sanya yara su shiga dakincan su fidda komai,zan din shiga ciki na kwanta goben ina tunanin zan riga kowa fita don ina da baqi a gidan baqi na”. Ba maina kawai ba,dukkansu sunsan wannan miqewar da yayi bawai ya yita bane saboda yana nufin abinda ya fada din,ya yita ne kawai saboda baya buqatar hada numfashi da maina,ya yita ne saboda isowar maina gurin,don a zaman tattaunawar da sukayi duka duka basuci koda rabin abinda suka zauna su tattauna saboda shi din ba.
Kaman yadda ya yiwa ama haka ya miqe cikin zafin nama ya tari gaban aba sannan ya sulale a gaban nasa.
“Waye wannan?,ku gaya masa ya matsa daga gabana!” Aba ya furta da wata irin kakkausar murya da duk sanda ta fita da irin wannan sautin……duk wanda ya sanshi to yasan cewa yakai maqurar fushinsa kenan
“Don Allah aba…..don girman Allah……!” Bai barshi ya qarasa magiyarsa ba sai saukar zazzafan mari da sautinsa ya karade falon. Kaf dinsu jini ya dauke a jikinsu,don ba wanda ya tsammaci irin wannan zazzafan hukuncin haka tashin farko daga wajen aba,kasancewarsa mutum ne bame yawan kaiwa koda yara hannu ba bare maina da a yanzun ya zama cikakken mutum
“Kaci gaba da tsayamin bisa hanya kaga yadda zamu kwashe dakai mahaukacin banza!……zaka matsamin ko sai na tattakaka a wajen?” Aba din ya kuma fadi cikin fushi. Cikin hanzari oncle umar ya miqe ya janye maina wanda ko gezau baiyi ba,hasalima baiso oncle umar din ya janyeshi ba,zaifi masa dadi ya barshi a wajen aba yaci gaba da dukansa wataqila ita daya ce sassauqar hanyar da aba din zaiyi saurin sassautowa ya saurareshi.
“Zauna nan,kada ka sake tsaiwa masa a hanya aliyyu” oncle umar da zuciyarsa shima ta fara motsawa ya fada cikin nasa fushin.
Kafeshi oncle umar din yayi da idanu,kaman yadda oncle bashar da oncle issoufou suka kasa motsawa,idanunsu dukka akan maina din,saboda wani abu ne da yazo musu a bazata gaba dayansu.
A hankali idanuwansa suke sauya launi saboda abinda ke motsa masa cikin zuciya,wani irin yanayi maras dadi qunci da zafin zuciyar da shi daya yasan me yake fuskanta.
“Yaushe ka dawo?, yaushe ka shigo gidan?” Oncle bashar yayi qarfin halin tambayar maina. Sanda ya dago fuskanshi da zummar amsa masa dukkansu saida kowa yasha jinin jikinsa. Wani irin yanayi fuskar tasa ta sauya,gaba daya kamanninsa sun canza.
“Yanxu oncle……yanxu na shigo,ama taqi saurarona tace saidai na sameku…… shima aba haka”
“Ba zasu saurareka din ba,don bakayi abinda zasu saurareka haka ta sauqi ba aliyyu” oncle umar ya fadi da wannan yanayin nasa dake nuna zafinsa. Idanu maina ya maida kan oncle umar din yana da zafi shima qwarai,har wani lokaci bibi ke ganin ta wajenshi ya gado zafi da kafiya,saidai nashi zafin da ya tashi ya ninka na dukka uwayen nasa. Duk da zafinsa idan ya gama spark ya sauka yana da budaddiyar zuciya,yana da zuciyar sauraro dake iya fahimtar mutum ta kuma bashi uzuri,yana da kafiya da qoqarin fahimtar da aba harma da bibi a duk sanda suka hau dokin naqi,ya hangi nasara ya idanuwa da bangarensa,don haka ya zamo a hankali ya gurfanar da kansa a gabansu
“Bansan da wanne baki zan fara baku haquri ba……bansan wadanne kalmomi ne zasuyi tasiri a kanku wajen wanke fushina dake zuciyarku ba…… abinda zan iya fada kawai shine……ina me neman afuwa da yafiyarku akan yanayin dana sanya zukatanku…..zullumi da fargaba dukka…….sannan gani a gabanku kuyimin dukka hukuncin da kuke ganin ya dace kan cutarwar da na yiwa jikarku” kalamansa sun dakesu sosai sun kuma sanyayar da jikkunansu. Dakin ya dauki shuru,kaman yadda basuce komai ba hakanan shima bai motsa daga tsugunnon da yayi ba,har sai da oncle umar ya magantu
“Koma ka zauna maina” kasa motsawar yayi yana jin nauyi da kunyarsu,yanajin nauyin abinda ya aikata din da yayi sanadin barinsa gida,yanajin kamar a yanzune komai ya faru,har sai da oncle issoufou ya kama hannunsa sannan ya matsa gefe ya sake zama sosai.
Fada sosai oncle umar ya balle masa dashi,don dama shidin baya barin ko ta kwana,sha yanzu magani yanzune ko akan waye,sai da yayi mai isarsa bashar da issoufou suna tayashi sannan ya rufe da fadin
“Abinda ya faru tsakaninka da matarka za’a iya cewa me sauqi ne inda ka zauna baka nuna ragwantaka ba…… za’a iya cewa rabo ne ya kawo haka,shi kuwa rabo baya tsallake rana da loakcinsa……ba kuma wanda ya isa ya hana wannan rabon fita sai ya fita a sanda ubangiji ya tsara……abu mafi muni shine tafiyarka,tafiya bata sati daya ko biyu ba,bata wata daya ko biyu ba,bata shekara daya ko biyu ba…..shekaru aliyyu,shekaru a qalla biyar?,wanne irin rago ne aliyyu?me yasa ba zaka tsaya ka fuskanci koma meye ba?,duk tsiya ba haramun dinka ka afkawa ba,me yasa ka tafi?” Ya jefa masa tambayar da alama tafiyar tasa tana daya daga cikin abinda ya sosai zuciyarsa.
Tabbas yasan cikin bacin ran dake danqare aran oncle umar ne kadai ya sanyashi ya jefeshi da kalmar RAGWANTAKA......saboda duk gidan yafi kowa sanin TSORO yana daya daga cikin abubuwan da bai baiwa muhimmanci a rayuwarsa ba JA DA BAYA basa daga cikin kafatanin dabi'unsa,duk yadda zai musu bayanin yadda yaji a sanda abun ya faru.....duk yadda zai kwatanta musu yadda qaddara ta dinga janshi tana tilasta masa ficewa daga gidan ba zasu gane ba.......daga bayan barinsa gidan kome daya faru dashi ya sakashi a mizanin wannan QADDARAR da tayi sanadin fitarsa a gida..... wanda yayi imanin banda hakan ta faru......da tuni a yanzun ba shine ALIYYU MAYAK'I da ake magana a kai ba,da tuni ba shine MAINA da yaketa qoqarin binne daukaka da matsayin da ya samu ba,bayan tarin qalubalen da ya gamu dashi sanadin fitarsa a gida
“Dukka ka yiwa kowa laifi,amma tamu me sauqi ce,kuma mun yafe maka,a yanzun babban qalubalenka, zamuyi iya abinda zamu iya wajen nema maka sasaauci,amma saukowarsu wannan tana hannunka,tunda bamu isa mu tilasta musu su yafe maka ko mu goge abinda ke ransu ba……” Ko iya wadannan kalaman na oncle umar kadai sun samar da wani sasaauci cikin gurbin zuciyarsa,sun kuma haifar da wani dan qaramin hope
Baisan ta yadda zai gode musu ba, matsayin nagartattun kawunnai a wajensa,ya miqe da zummar barin falon,yana kuma wassafa ta inda zai fara tunkarar wannan gundumemiyar matsalar........ babban yaqi da zai zama madubin rayuwarsa muddin ya cimma nasara.
“Kaje zuwa da safe koma meye zamu qarasa magana akai……gobe daurin auren qannenka biyu”
“Waye da waye?” Ya samu kansa da jefawa oncle umar tambayar saboda wani fargaba daya kamashi. Dukka sai suka dan tsaya suna dubansa kafin oncle umar din ya bashi amsa
“Aminata da yasmine” qas yayi da kansa kuma yana jin nauyinsu,yana jin kamar yayi tambaya akan makomar aurensa da sultana……to amma kuma hakan kamar zai zama da gaggawa,karbarsa da sukayi bawai yana nufin yanzun shi bame laifi bane a wajen kowa ba…… a’ah……yasan sun karbeshi ne saboda tsananin zumunci irin nasu da yadda suka tashi da soyayyar junansu data yaran da suka fita daga tsatsonsu.
“Aliyyu” oncle issoufou ya kirayeshi da sassaucin nan nasa,don shi din mutum ne da bashi da zafi sam,duk cikinsu yafi kowa sanyin hali
“Ka kama bibi,ka tabbatar ta zame maka tsani” kai ya girgiza wani busashen murmushi na fita daga saman labbansa,tamkar oncle issoufou din ya shiga zuciyarsa,bibi ce kawai last hope dinsa da yayi imanin tana da power din da zata maida komai bisa saiti,ko meye zatayi duk wani borenta bazai bari ya dameshi ba,zai runtse idanunsa,zai kuma gwada mata shi dan yau ne,domin yasan halin bibi sarai,zuma ce sai da wuta,amma kuma yana da babban yaqini a kanta.
Daidai inda sukayi kacibus ya kalla sanda yake fita a falon,yaja dogon numfashi daya sauka har tsakiyar hunhu da zuciyarsa
“SULTANA” ya maimaita sunan kamar yaune ya fara jinsa. Akwai babban game tsakaninsa da ita,yana tunanin itace abu na qarshe da zai cimma,a yadda ya tsara itace zata kasance matakalar qarshe,yaya zaije mata?,ta yaya zai risketa?,dukka bai san wannan ba……abu daya ya sani,ya kuma haqiqancewa kansa shine……..duk RINTSI……duk yadda za’a je a dawo ba zaya taba yarda da abinda zai shafi igiyoyinsa ba
“Idan suna nan har yanzu?” Wani sashe na zuciyarsa ya jefa masa tambayar data tilasta masa riqe hannun almu dake zaune zuwa yanzu a gefan qofar falon saman wasu qananun kujeru dake wajen don ya gaji da tsaiwar jiransa
“Idan har yanzu sashe na yana nan……ina buqatarsa,ka gyaramin koda iya wajen da zan ajjiye kayana” ya fada adan birkice,don har yanzun bayajin cikakkiyar nutsuwa a jikinsa. Kai almu ya gyada yana miqewa,har yayi taku biyu mainan ya kirashi,sai ya dawo ya tsaya cak gaban maina yana kallonsa
“Bayan tafiyata ciwon kurumta ko bebantaka ya sameka ne?” Ya masa tambayar yana duban idanunsa. Kai ya girgiza sannan ya matso taku hudu da sauri ya fada jikin mainan yana cewa
“Barka da dawowa ya maina,Tu nous manques(munyi kewarka)”
“merci(na gode)” ya ambata da raunanniyar muryar nan yana daga almu daga jikinsa yana kallonsa. Shima almu din kallon fuskar maina yakeyi,yana mamakin yadda ya mainan nasu ya sake komawa. Babban mutum da wani irin shinfidadden kwarjini da nutsuwa saman fuskarsa. Abinda shima maina ke wassafawa a ransa kenan,almu din da ya tafi ya bari da sauran quruciya ya zama saurayi
“Ka girma almu,ina fata zaka taimaka wajen kawo wani haske komai qanqantarsa tsakanina da ama”
“je promets in sha Allah(nayi alqawari in sha Allah)” kai maina ya jinjina,yana a tsaye har almu ya tunkari tsohon sashensa da baiga wani abu daya sauya ba ta wajen,saima gyara da wajen ya samu da kuma kulawa.
A yadda idanunta suke a rufe sam bataga bibi dake zaune cikin falon ba tana kallo saboda raguwar jama'a daga sassan nata. Sanda ta shigo din daga kai kawai bibi tayi ta bita da kallo,yanayin taku da tafiyar sultanar dukka ba sune tattare da ita ba
“Ikon Allah” bibi ta fadi har zuwa sanda ta tura qofar dakin dake kusa da ainihin dakinta ta shige
“Allah ya kyauta…….itama wannan ja’irar na fuskanci ta zama baudaddiya” ta fadi a bayyane tana maida toothpick din data zaro bakinta taci gaba da sakacenta.
Kamar daga sama taji sallamarsa,saita maida dubanta da hanzari bakin qofar qawataccen falon nata. Yadda ya zuba mata idanu haka itama ta zuba masa tana jin kamar cikin mafarki take ko kuma majigi take kalla
“Wannan kamar maina” ta fadi cikin tantama duk da yaqininta yafi yawa akan tabbas shi dinne. Qafafunta dake saman kujera ta sauke,har yanzu bata dauke dubanta daga kanshi ba kamar wadda taga fatalwa. Ta waiwaya kadan tana qwala kiran sunan
“Tanja!,ke tanja!!” Tanja tana kusa,don tana kitchen din bibi din zata zuba abinci taci,saita saki abinda takeyi din,don yanayin kiran da bibi ke qwala matan baiyi kama da kiran lafiya ba,uwa uba kuma tanata juya dawowar maina a daidai wannan lokaci.
Dashi idanunta suka fara cin karo,yana tsaye abinsa qyam daga bakin qofar,a dan rude ta kalli tanja
“Wancan dake bakin qofar a tsaye ba aliyyu maina bane?” Tayi tambayar bihaqqi tana neman sani.
Tanja bata ma dubi wajen ba ta bawa bibi amsa
“Shine” kammala fitar haruffan guda biyar yayi daidai da miqewar bibi tamkar bame fama da ciwon qafa lokaci lokaci ba,sai kawai ta soma jan zaninta tana daurin qirji dashi idanunta fes bisa fuskar maina da sai data miqe din take sake qare masa kallo abinda daga maina din har tanja suka gaza gane abinda take nufi da hakan
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 54
Idanunsa fes bisa kanta,yasan dukkan wani kalar rigimarta,yasan meye zata iya aikatawa da wanda ba zata iya aikatawa ba,yasan kuma lagonta qwarai da gaske.
“Billhuwallazi lailah illa huwa idan ma fatalwa ce ba aliyyu ba ni bibi nafi qarfinta…….idan kuma har da gaske kaine…….da idanuwanka guda biyu a bude na rashin kunya ka iya dawo mana cikin gida to dai dai nake dakai,shege ka fasa ni da kai” ta fadi cikin daukaka murya tana sake gyara daurin zaninta da kyau tamkar me shirin yin dambe dashi. Dolen dole badon yaso ba murmushi ya subuce masa yana kallonta,da gaske take tattara dukkan qarfinta kamar wadda ke shirin yin dambe da qaddararta.
A yanzun ba bibi kadai ba, kusan duk wanda keda ruwa da tsaki da rayuwarsa yasan a tunzure yake dashi,bazaiyi wani abu kuma da zai sake tunzurata din ba don yanzun tamkar itace sitiyarin gidan gaba daya,samun kanta shine samun kan kowanne mutum dake cikin gidan,don haka yaci gana da takawa yana nufarta
“Au……ba zaka dakatamin a nan ba?,la’ilaha illallahu……da gaske dai aliyyu ne!, jama’a kuzo ku ganemin ikon ubangiji na” ta sake fada cikin daga murya tamkar tanasom tara masa jama’ar gidan gaba daya
“Bibi kibi a hankali,ba fatalwa bane na gaya miki maina ne” tanja ta furta adan daburce ganin yadda bibi ta dage lallai saita hada masa jama’ar gidan. Shikam ko gezau be fasa takawa zuwa wajenta ba,yayin da taci gaba da kwakwazo da jan salati iri daban daban.
Yana isa dab da ita baiyi wata wata ba ya sanya hannu ya riqeta da kyau
“Sakeni,sakeni nace” ta fadi yana qoqarin qwace hannunta daga nasa cikin fada da hargagi
“Kiyi a hankali,tunda dai baki samu damar hadamin jama’ar da kikayi niyya ba aisai ki haqura ki zubawa sarautar Allah ido ko?” Ya fadi yana qoqarin zaunar da ita. Dukka sauran qarfinta ta sanya ta tureshi cikin fusata tana cewa
“Gafara can ka bani waje,wato nice marainiyar wayonka,ka tsallake katanga.ka shigowa mutane cikin gida a sirrance zaka zo.ka cuceni,banga alamar akwai wanda yasan da shigowarka cikin gidan nan ba” qaramin murmushi ya saki yana sake yunqurin riqota
“Allah ya kiyaye…….da lalacewa ta sameni,na gudu daga gida……na tashi dawowa na biyo ta katanga?…..ai kuwa da nayi asarar suna,kuma da daga yau na ajjiye sunan Aliyyu na koma aliya”
“Ahaf…….lalacewa kuma ta nawa?,duk dan da zai tsallake albarkar iyayensa yabar gida shekara da shekaru ai lalacewa ta gama samunsa” ta fada tana sake qoqarin tureshi . Har cikin zuciyarsa maganar tata ta bashi dariya,saidai boren nata yayi imanin mataki ne na nasara,nasarar da ya tabbata tana da alaqa da addu’ar da ya tsananta yi tun kafin ya sanya qafafunsa cikin gidan.
“Kina batan lokaci ki zauna ki marabceni kawai” ya fadi yana sanya qarfinsa cikin tausasawa ya maidata ya zaunar saman kujera,sai ya waiwaya yana duban tanja
“Jeki abunki kija mana qofa miji zai gana da matarsa” dan qaramin murmushi me hade da hawaye ya qwacewa tanja,tayi missing maina qwarai,bama ita ba,kowa dake gidan idan zaiyi magana ta tsakani da Allah zai fadi haka. Duk da zamantowarsa me zafi fushi da kuma zuciya……amma kuma shi din mutum ne me dadin mu’amala qwarai da gaske.
Gadon bayansa ta kaiwa dundu da dukka qarfinta tana fadin
“Allah ya kiyaye Allah ya sawwaqe nayi miji da kai,mijina jarumi ne,bai tana ja da baya ba” ta fadi tana yarfa hannunta,don dukan data kai masan ba shine yaji zafin ba itace taji,ita dimma bata ankara da wautar da tayi ba na kai masa dukan sai daya zauna ya babbake a gabanta sannan ta qare masa kallo tsaf. Ya zama ingarma dake da wani irin ginanne kuma tsayyen jiki da nuna zallar qoshin lafiya da cikakken qarfi,ko ina a murde alamun daga qarfe sosai sun bayyana ga jikinsa,duk da cewa cikin sutura yake cikakkiya.
“Bafa mainan da kika sani a baya bane kike dukana haka bibi?”
“Na sani mana…..wannan wani shashashan maina ne,gudajje daga gidan iyayensa bayan yaso ya kashe ‘yarsa kuma ‘yaruwarsa sannan matarsa” ta fadi masa cikin fushin zuciya,tana jin takaicin yadda bata da cikakken qarfin tureshi ta tashi a wajen ta daina kallonsa. Wani qasaitaccen murmushi ya saki yana sadda kanshi qasa kafin ya dagoshi
“Kowa na gudu…..kowa guduwa nayi…….bien(da kyau),duk kuci gaba da fada,ba laifi tunda abinda idanu suka gani kenan,amma nan gaba kadan zan tabbatar muku da sabanin fahimtarku” ya qarashe maganar yana jan siririn hancinta me tudu kadan wanda kusan dukansu irinsa suka gado,wani irin hanci me kyau dake qarawa fuska kyawu.
Hannunta ta saka ta buge hannunsa tana cewa
“Ka fita ka bani waje tun banci mutuncinka ba,ko kuma na kira ubanka ya fiddamin da kai,tunda naga alama shi kake tsoro” idanu ya fiddo waje,sai ya sulale qasa yana riqe dukka qafafunta hadi da dora kansa saman qafafunta,yayi laushi qwarai da muryarsa cikin sigar tausayi
“Indai ba bindigeni kikeso aba yayi ba kiyi haquri kada ki kiramin shi,dazun nan ya gama kwakwadamin mari,bibi kaman zai tsinemin,ama taqi koda kallo na,kema nazo kin juyamin baya bayan ko meye ya faru ke kika dauremin qarqashin aikatawa…….” Bakinsa ta kaiwa bugu da sauri,saidai kuma bata sameshi ba don ya kauce yana boye dariyar dake subucewa tun daga zuciyarsa,fiye da rabin tsoro razani da quncin da yake ciki a yanzun baya jinsa tunda gangar jikinsa ta gamsu da cewa yana cikin gida…… yana cikin family dinsa,yana cikin ahalinsa iyalinsa
“Ni nace kaje ka yiwa diyar mutane fyade?,ka kusa kasheta?,ka illata mata idanu maina?” Ta fadi adan rude. Maganarta ta qarshe ita ta dakeshi,har ta sanyashi daga idonsa yana kallonta,dan siririn murmushin da ya soma samu saboda tubura bibi da yakeyi ya bace bat daga saman fuskarsa
“Illata idanu bibi?, yaushe?,garin yaya?” Tambayar tasa ta sanyata daga hannuwanta dukka biyun ta zuba masa ranqwashi da qasusuwan yatsunta da dukka qarfinta,ta yadda tazan zafin zai ratsa tarin sumarsa ya kuma isa ga ainihin tsakiyar kansa. Idanunsa ya runtse gam,saboda da gaske zafin ya isa har fiye da inda taso yaje din
“Ni zaka yiwa tambayar yaushe ka illatata din?,sanda ka aikata aika aikarka wa kayi shawara dashi?,oh…..ni ‘yar nan naga ta kaina……ban sake yarda lallai baka da kunya ba sai yau aliyyu……tashi ka bani waje,kada ka sake shigomin guri,ban gayyaceka ba,daka dawo bani ka dawowa ba,tashi nace” ta fada tana tureshi da gasken gaske. Yaga fushi da motsuwar bacin rai saman fuskarta,amma kuma ta wani sashen da batayi zato ba akwai farincikin ganinsa danqare qasan zuciyarta wanda batasan wannan hasken yana bayyana akan fuskarta ba.
Tsam ya miqe din yana dubanta na wasu sakanni ya qare mata kallo,sai ya zuba hannayensa a aljihun wandonsa yana magana a nutse,duk da qasan ransa akwai razanin jin cewa ya yiwa idanun sultana illa,saidai yana mamakin ta ina?,don baiga wani nakasu cikin fararen zagayayyun idanun nata data jefa masa kallo dasu a makka da kuma dazu dazu ba cikin falon aba
“Zan tafi bibi,amma bawai na tafi kenan ba,zan dawo koda zaki yayyanka ni ki sakani a tukunya…….kafin na karbi kowanne hukunci ya kamata a bani damar magana koda ta minti daya ne,zan bayyanar da kaina a gobe gaban kowa,zan kuma karba kowanne hukunci da kuke tunanin na cancanci ns karbeshi” daga wannan ya soma takawa don barin falon,amma kuma idanunsa manne da bakin qofar dakin,dakin da bazai taba mancewa dashi ba……dakin da yasha mafarkin gashi a cikinsa…..wancan din daya faru yana maimaita kansa har sau babu adadi…..cikin kowanne dare da zaizo ya shude. Cikin jikinsa ya dinga ji tana cikin dakin,amma koda wasa bibi na wajen bazaiyi gangancin shiga ba,a yadda take a fusace ya tabbatar tana iya tayar da boren da a yau aba da bibi ma basu isa sunyi bacci cikin gidan ba.
Dai dai lokacin daya fita din ta sulale qasa tana jingina bayanta da qofar dakin bayan ta gama kallon komai dake faruwa tsakaninsa da bibita qaramar hudar da akayi don hangen wanda ke waje. Tana ganinsun,amma kuma bata iya jin abinda duke fadi a tsakaninsu. Tun dazun hawaye ya gama wanke mata fuskarta gaba daya,saita qarasa zama dirshan qasan dakin tana rufe fuskarta da dukka tafukan hannayenta.
Duk da batajin me bibi ke gaya masa amma kuma sai tayi mamakin yadda bibin ta tsaya saurarensa koda kuwa kanainayetan yayi. Ta dauka zata sanya qafa tayi fatali dashi,ta zaci zata sanya madoki tayita dukansa har sai ya fice musu a daki da qafafunsa,duk wani action na bibi bai burgeta ba duk data fuskanci bore tayi masa,so tayi bibin ta masa irin tarbar da zaiji baya da sauran sha'awar sake zaman gidan.
“Ke sultana!…..,kukan meye kikeyi?,kin manta yanzun ke ba sultanar baya bace?,kin manta a yanzun ke wata sultana ce ta daban?,a baya min xubda masa hawaye,a yanzun bai cancanci kici gaba da xubda masa wannan hawayen ba,ki qarafafawa kanki gwiwa,ki gayawa kanki da kanki a yanzun damuwa bata cancanceki ba…….kiyi moving forward,kada ki bari ya sake maidoki inda kika riga kika wuce” kaifafan maganganun da suka dinga kai komo kenan a tsakiyar qwaqwalwarta.
Sosai taji ta gamsu,ta yadda yanzun shi din ba kowan kowa bane cikin rayuwarta,bashi da kaso ko misqala zarratin a rayuwarta,me yasa zata bari ya dameta?. Da wannan tunanin ta isa gaban madubi tana kallon kanta da kanta. Da gaske ta canza,da gaske ba sultana yarinya qanqanuwa bace wadda zai yiwa qarfa qarfa......wadda zai yiwa.kama.karya......wadda zai yiwa dukkan abinda yaga dama yakeso,a yanzun ta girma......ta kuma mallaki hanakalin kanta,koda jama'ar dake kewaye da ita wadanda zata rayu dasu sai wadanda taga damar zama dasu ta kuma zabesu.
“Dole ya sani ya kuma shaidawa kansa da kansa da da yanzu ba daya bane” ta furta a fili qasa qasa tana motsa jajayen labbanta. Bandaki ta shiga,ta raba kanta da kayan jikinta ta watsa ruwa hade da alwala. Sakakkun kayan bacci ta saka don tafi sakewa,duk wani motsi nata tana furta
“La’ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin” saboda zuciyarta tayi sanyi. Hijab ta sanya har qasa,ta isa qofar dakin nata ta murza key don kada ma su dawo su dameta,tun dacan dama bata kwana da kowa dakinta don batason takura ko hayaniya,yanzun ma bata son kowa ya dameta shi yasa ta rufe dakin,ta shimfida abun sallah tahau ta kabbara salla shafai ds wuturi sannan ta dora da nafiloli.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 55
Idanunsa suna kan kowanne sashe na sassan nasa,yana nan kaman yadda yake,ba abinda aka sauya ba kuma wani abu daya lalace kamar bai dauki wadannan shekarun baya nan ba.
Duk inda ya gifta ba abinda ke dawo masa sai shekarun samartakarsa, abubuwa da yawa ya dinga tunawa har ya ratsa falonsa yakai ainihin bedroom dinsa.
Yana shiga almu yana ajjiye mop stick din daya gama goge masa tiles din wajen,suka hada idanu da maina din,sai yadan sadda kansa kadan. Abun almu din yana dan bawa maina mamaki,duk ya maidashi wani baqo qarfi da yaji,duk da ko a baya ba sakewa tsakaninsu sai desipline,amma kuma yana tunanin kaman a baqon almu yake kallonsa.
“Ina goumar?” Ya tambayeshi, tambayar data sanyashi daga kai ya kalleshi,don a nasa lissafin maina din bai wani san goumar can can ba
“Sunje niamy…..amma gobe da sassafe jirginsu zai iso da angon yaaya aminata” kai ya jinjina,shuru na wasu ‘yan mintuna ya biyo baya,sai ya gyada kai
“Shikenan jeka,sai da safe”
“Akwai wani abu da kake buqata?” Almu din ya tambayi maina,har qasan zuciyarsa yana jin tausayinsa,duk da baikai wayon haka ba sanda yabar gida amma kuma yana iya tuna kulawa da yake basu,sa’annan a yanzun ya san cewa gagarumin qalubalen dake gaban yaa aliyyun,duk wata kulawa bazai sameta daga iyayensu ba
“Babu” ya amsa masa a taqaice
“Merci” ya sake fadi yana jin dadin yadda almu din ya nuna masa kulawa. A yadda yakeji din baya jin zai buqaci wani abu,nutsuwa kawai yake da buqata da kuma kebe kansa har zuwa safiya. Don haka almun yana fita ya soma zagayawa cikin dakin,yayi ‘yan dube dubensa. Komai yana nan hatta da suturunsa ba abinda aka taba,ya maidasu waje daya ya killace,don a yanzun bazai iya amfani da ko daya daga cikinsu ba.
Kayan jikinsa ya cire ya daura towel ya wuce bandaki. Ya jima yana dumama jikinsa sosai, tunani cunkushe a kwanyarsa. Baisan yaya safiyar gobe zata waye masa ba,baisan da wanne ido da kuma wanne hannu zasuci gaba da tarbarsa,saidai koma meye yana bawa kansa tabbacin juriya da dagewa hadi da jajircewa.
Kayansa da yazo da su ya bude,ya fidda pajamas marasa nauyi ya saka,kwanciya yakesonyi amma bayajin zai iya kwanciyar,don haka ya shimfida abun sallah shima ya kabbara sallah da tarin buqatu dake cikin ransa.
*Tun asuba hayaniyar cikin gidan ta qaru saboda yawan jama’a da kuma hada hadar daurin aure da aka fara yi,wanda duka daurin auren su biyun zai gudana ne a babban masallacin alhj Mohammed mayak’i dake farkon street din nasu.
Tana idar da sallah ko hijabin jikinta bata fidda ba ta koma saman gado,idanunta fal da bacci don a jiya bata samu cikakken bacci ba.
Batasan adadin awannin data shafe tana bacci ba,ta daiji anata knocking sama sama amma bata ko motsa ba,don tasan mutane ne kawai zasu dameta,saidai a yanzun bugun da ake mata yasha banban da wadancan,don yanzun kamar za'a tsinke qofar a shigo,dole ta miqe tana lalubar dankwalinta da ya zame ta sanyawa kanta,sannan ta sauko daga saman gadon ta nufi qofar.
Yasime ne a tsaye,tayi kyau cikin shigar wani arnen farin lace da ya wadatu da ado da duwatsu masu qyalli,kana kallonta basai an gaya maka ba amarya ce, fuskarta ta dauki makeup sosai wadda ta sake bayyana ainihin kyan nan nasu da sukayi gado. Houda na tsaye a gefanta cikin army green shadda da sukayi anko dukkansu 'yammatan amare suka tsara zasu sanya a yau din. Wata harara ta jefa mata
“Wai bacci ma kikey?” Hannu ta sanya tadan dafe kanta
“Da ciwon kai na kwana Yasmin,don Allah karkiyi qorafi” ta fadi tana karya murya. Dariya ta bawa Yasmin din
“Kiyi ki shirya don Allah,kada azo daukan hoto bake a ciki”
“In sha Allah” ta amsa mata,wanda ita kanta tasan ta amsa mata ne kawai,amma sam yau bata sha’awar fita ko nan da can. Harabar gidan gaba daya bata burgeta,ta tabbatar a yau din kusan labarin da zaiyi trending cikin gidan shine labarin dawowar maina. Suna juyawa tana shirin maida qofar ta rufe tanja ta qaraso
“Ama tace na dubaki kin tashi?”
“Na tashi tanja……don Allah tea nakeso me dumi sosai,madara da sugar kadan”
“Tea kawai?” Kanta ta gyada mata tana lumshe fararen idanunta,bakinta babu test kwata kwata,shima tea din zata sha ne kawai maganin yunwa.
Tanja tana fita ta juya ciki ta soma zare kayanta ta fada wanka. Koda ta fito tanja ta aje mata tea din,sai ta zauna ta fara kurba a hankali tana dumama cikinta. A hankali sai tunaninta ya koma daren jiya,wata siririyar faduwar gaba ta ratsa qirjinta,ta maida idanunta ta lumshe tana son kauda surar fuskarsa dake gilma idanunta. Benazeer da batoul ta tuna,wannan ya sanyata ajiye cup din a hankali,ta jawo hijab ta zura ta nufi qofa. Tana gab da fita a dakin wata murya daga can qasan zuciyarta ta jefa mata tambaya
“Idan kinje gurinsun me zakiyi?,zaki hanasu yawo ne bayan gidan cike yake da yara?,kada kiyi abinda mutane ko shi kansa zaiyi tsammanin kin damu da sha’aninsa ne,bake daya ba,akwai dakaru a gabanki da bai isa yace zaya dauki yaran ko ya aiwatar da wani abu ba” ajiyar zuciya me nauyi ta sauke sannan ta dawo da baya jiki a salube,daga tsaye ta dauki tea din ta kurbe,saita koma wajen drawer dinta ta soma duba kayan da zata saka, zuciyarta da tunaninta haka kawai ya raja’a akan yaran.
Tun asuba yayi alwala ya kuma fita sallar asuba kamar yadda kowanne namiji dake gidan yakeyi tun gabanin barinsa gida,har kuma yanzun babu abinda ya sauya. Yana qoqarin fita daga makeken gate din gidan sukayi kacibus da aba adan hanzarce,da alama shima yaso ya makara ne. Idanu suka hada da aba din,sai ya janye idonsa tamkar ma baisan mainan ba,ya kuma qara taku ya wuceshi a sanda maina ke yunqurin yi masa magana. Ajiyar zuciya me sanyi ya sauke yana lumshe ido hadi da budeshi,wannan abun idan aba yana masa shi yana sanyashi jin tamkar zai mutu. Ba haka ya saba masa ba,a shekarun baya kafin komai ya faru idan sukayi kacibus irin hakan da hannu yake masa nuni da ya matso,idan ya matso din kuma sukan wuce masallaci tare da aba din kafada da kafada,a yanzu da yake ganin akasin hakan sai yakejin kamar zuciyarsa zata tsinke daga qirjinsa,bazai iya jurar wannan halin ko in kula na aba ba. A baya yaci gaba da bibiyarsa har suka isa masallacin,sanda aba ke qoqarin kafa sahu cikin zafin nama ya tsaya daga gefansa,ya kuma daidaita sahunsa dana aba din. Yayi zaton zaiyi wani motsi amma sai yaga ko daga kai ya dubeshi baiyi ba,tamkar ma baisan dashi suka hada sahu tare ba.
Suna idar da sallar aba din yadan ja gaba ya fita a sahun,sannan ya zauna sosai ya fara azkar din daya zame masa.jiki duk safiya muddin yana da lafiya,idan kuma baya dan jin dadi yana komawa gida yayi cikin falonsa balcony ko bedroom dinsa.
Daidaikun mutane da sukasan maina sai suka dinga matsowa suna gaisawa dashi tare da tambayarsa yaushe ya dawo qasar,saidai ya danyi murmushi yace musu
“Jiya” yadda suka dinga masa barka ya alamta masa lallai sunyi zaton karatu ya tafi. A hankali a hankali yana gaisawa dasu har zuwa sanda suka kammala,ya dan juya idonsa kadan ya saci kallon aba. Yadda yake tun dazun har yanzu a haka yake a zaune,yaja numfashi sosai,sannan ya miqe cikin mazantaka ya taka izuwa garesa.
A gabansa ya zube gwiwoyinsa,muryarsa cike da girmamawa da kuma rusunawa ya furta
“Barka da asuba aba” idan carbin dake hannunsa ya amsa shi shima haka,sai yaci gaba da jan tasbaharsa baiko motsa ba bare maina ya sanya ran ya jishi. Sake maimaita gaisuwar yayi,wanda yana direta aba din ya yunqura ya miqe yana durfafar qofa,baiyi qasa a gwiwa ba ya take masa baya,saidai kafin ya cimmasa har ya sanya slippers dinsa masu tsananin taushi ya soma barin farfajiyar masallacin.
Dab da zai fita ya cimmasa,ya sake taresa karyar da wuya dama murya gaba daya
“Aba…….na roqeka don……”
“Bakaji abinda na gaya maka ba jiya?,kai wanne irin mahaukacin yaro ne?, meye alaqata da kai da zaka dinga bibiyata haka?,ni bani da wani d’a me kamanceceniya dakai,ka fita daga harkata tun kafin na saka hukuma su kamamin kai” yayi maganar a fusace yana nunashi da yatsa,sannan ya kewayeshi yana wuceshi bayan yaja dogon tsaki. Sosai jikin maina yayi sanyi,abinda yake gani a idanun aba din me girma ne,anya zaici gaba da tunkarar aba?,anya ba bibi bace kadai tsaninsa kaman yadda oncle issoufou ya gaya masa?.
Cikin qarfin hali yaci gaba da takawa cikin gidan. Koda yakai bai koma sassansa ba sai ya zarce sashen ama. Can dinma mutanen daya samu a sassanta wadanda suka tattashi sallah dukka basu koma ba binsa suka dinga yi da kallon yaushe gamo?,ya gaisa da wadanda zai iya gaisawa dasu,ya tambayi bilki me aikinta ta gaya masa yanzun ta shiga daki.
Sau uku yana knocking sannan ya murda qofar,bakinsa dauke da sallama,qasan zuciyarsa cike fal da addu'a. Da ita ya fara tozali,tana zaune saman tattausan abun sallarta dinnan,jikinta sanye da ustazah hijab da skirt dukkansu kala me haske. Tsananin tsafta da gayunta ya santa kusan komai nata me hasken kala ne,sai dai daiku masu duhun kala. A nutse ya qaraso cikin dakin,ya kuma yiwa kansa mazauni a qasan dandagaryar turkey carfet din dake malale a dakin wanda ya qarawa dakin kyau da kuma tsari.
Hannayenta a sama tana addu'a,sai shima ya buda nasa tafukan hannayen,sanda ta kammala suka shafa a tare,sannan ta waiwayo suka hada idanu.
Kwarjinin nan nata yana nan,gaba daya fuskarta ta cika da hasken ibada sanin kima da martabar kai. Wani lokaci su uncle abdulhakeem kan bata lokaci kan cecekucen kwarjinin da yayo gadonsa yayi,amma basusan tsakanin hamid da hamdiyya waye yafi wani kwarjini ba?.
Sai data gama zuba masa dukka dafin kwarjinin idanunta sannan ta janye daga kallonsa. Zuciyarta na hira a kansa ita kadai. Mainan nata ya girma,ya zama cikakken mutum wanda ta tabbatar akwai maganganu masu yawa da labarai cikin tafiyarsa da kuma dawowarsa,saman kowacce fuska akwai labari......cikin kuma kowanne littafi nan ma tasan akwai labari,amma a yanzu bata jin zata bashi wannan qofar ko damar haka a kurkusa. Kaman yasan niyyan tashi ta bashi waje takeyi sai yayi caraf da dukka hannayenta ya kuma hanata miqewar,koda ta daga kai ta kalleshi sai ta tsinci hawaye fal idanunsa. Kuka a idanun aliyyu?,abinda zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba gani ba,tun yana qaraminsa kuka abune me wuya a wajensa bare kuma sanda ya mallaki hankalin kansa,yana da tsananin fushi kafiya da zuciya,wannan ya sanya ko yara sa'anninsa basu fiya takalar fada dashi ba,idan kuwa kayi gangancin yin hakan kaine zakasha qasa
“Don martabar fiyayyen halitta ama kada kiyimin haka,aba haka yakemin tun jiya,kema haka zakiyimin ama?,idan duk duniya sun gaza fahimtata ama na dauka ke zaki riga kowa fahimtata,ke zaki fara sauke fukafukan jin qanki a kaina ama?,ban tafi don wata manufa ba,banyi nesa daku saboda na rainaku ba…..hasalima nayi nesa daku ne saboda kunyar keta maganarku……saboda kunyar na aikata abinda ya kamata ace ya zama sirri ne tsakanina da ita saidai nayi ta yadda ya zai fita,na tafi ne saboda bansan da idanun da zan kalleku ba,bansan da bakin da zanyi muku bayani ba……ama……. wallahi wallahi wallahi ban tafi da nufin na tafi daga gareku kenan gaba daya ba…….na tafi ne da niyyar idan kun huce zan dawo……a raina ban taba sakawa zan tafi nayi koda wata guda ba…….sai kuma gashi komai ya sauya……ina biye daku ama……ina biye da duk wani motsinku ama…….ban yanke daga shiga rayuwar sultana tare da sanin hakinda take ciki ba ama……amma kuma saidai a cikin tarko nake……ina cikin wani dauri da muddin na bayyana a gareku rayuwata na cikin hadarin da bani da gatan da zai fiddani…. Lokacin kuma da nake tunanin na zama free……ina da ‘yanci sai yayi dai dai da lokacin da zan cika BURIN ABA…..MAFARKIN ABA…..burin dana tabbata a duk sanda na bayyana a gabanki babu shi kema zaki qalubalanceni BABBAN LIKITAN ZUCIYA kuma DAN KASUWA CIKAKKE…..Na hadu da jarrabawar da na tabbatar barinku ne sila……na kuma hadu da lalurar da afuwarku da kuma yafiyarku ne kawai zai bani maganinta……” Hannu ta daga masa tana yin qasa da kanta,batason yaga zallar rauni da karaya daya zubawa zuciyarta,batason yaga tausayin daya lullube qirjinta,irin tausayin da dukka uwa keji akan d’anta komai girman laifi ko kuskurensa,saboda kasantuwar zuciyar mahaifiya ta banbanta da zukatan mutane gaba daya,koda kuwa ita wannan uwar wata halitta ce daban bata dan adam ba……
“Banason naji komai daya faru dakai,koda zanjin zanji ne a tare a kuma lokaci guda da mahaifinka,kaje ka nema yarda mutum ukunnan…….sannan ka dawo gareni” sai ta zame hannunta tana miqewa.
Shima bai zauna din ba sai ya miqe yayi tsaye yana kallonta tana barin dakin
“Kiyimin alfarmar amsa gaisuwata ama…..koda iya ita kadai na roqeki” har ya fidda rai don takawa take tana barin dakin,kamar kuma ba zata amsa ba,dab da zata fita din tace masa
“Nayi maka” cikin dubunnan nauyikan dake qirjinsa yaji kaman an cire daya,ya fesar da iska me nauyin gaske da ya fusgota daga cikin cikinsa yana aza tafin hannunsa saman fuskarsa wani farinciki yana dan ratsashi,sa’annan yana jin qwarin gwiwarsa ya sake qaruwa. Sai daya ji ya nutsu sannan ya soma fita a dakin,cikin takunsa me cike da qasaita,saidai kuma a yau din a sanyaye yake takawar.
Bangaren bibi ya nufata kai tsaye,shikam a yau yakeson gamawa da bibi din,don dama bai azata a ma’aunin matsala ba,ya duba agogo dab da zai shiga sashen,ya kwasarwa drama dinta awa daya kacal,don yanason ya koma bangarensa ya sake runtsawa koda na awa daya ne sannan ya shirya ya fito,don yanason ayi daurin auren ‘yan uwansa dashi.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
ZAFAFA FAMILY na maraba daku🫂🫂🫂🫂🫂
146
Mam a ranar daya cika kwana hudu a asibiti Omar ya bada umarnin kawai a miqasa asibitin mahaukata sbd cigaban da Babu ko kadan a tattare dashi sbd duka matakin dayaso dauka ma akansa ganin yanda gaba daya fatar jikinsa yayi Wani mummunan baqi a Cikin kwana hudun sbd balain ruwan alluran da suka shigesa Wanda likitoci sun tabbatarda qwayoyin Cikin ruwan alluran sun Riga sun kama ruwan jikinsa sedai idan zaa fiddasa waje ne.
Ahmed baima bari Omar ko Jamaal sunji wannan sakamakon ba ya sanar da Dad Omar abinda zai sanar Anan ne Omar din yace a miqasa asibitin mahaukata kawai.
Jamaal kuwa baima San meyake faruwa ba sbd ya Riga yabarwa Dad Omar din yaji da komai.
Haka aka nade Mam din da idonsa daya aka kaisa asibitin qazanan mahaukatan Dake wajen gari aka basa daki bayan an cike masa komai.
Yanaji Yana Gani baya iya magana bare motsawa aka ajiyesa da Ido daya tsiyaye aka barsa Cikin dakinda gwara wata bolar dashi sbd tsananin wari da sauro ga Kuma wasu ruwa Dake kwance gefen dakin wainda har sunyi baqi da alama ruwan sama ne ke zubowa idan anyi Suna taruwa aciki.
Ko ficewa Basu gama yiba sauro da quda suka fara yayyabesa daga kwancen dayake.
Sama ya Dan kalla ahankali yaga Babu ko ceiling take wasu hawaye masu radadi da Ciwo suka gangaro gefen Idanuwansa Yana rufe Idanuwansa yanajin wasu irin qwari ja shigewa rigar jikinsa da ko ita Bai samu an sauya masa ba duk jinin daya zubar mata ya bushe yayi Wani irin baqi.
Duhun dakin kadai idan dare yayi wata azabar datake firgita ruhin dan Adam dayake cikinsa ne,
Sanyi jikinsa yayi Yana sake rintse Idanuwansa hawayen cikinsa suka gangaro sbd yasan har abada bazai taba qara moruwaba sbd shi kadai yasan azabar dayake ji a jini da jikinsa.
Dare nayi gurin ya dauki tsit bayan kukan sauron masu yawan gaske dayake tashi a dakin Babu sautin komai,
Wasu azababbun cinnaku ne ke cizonsa Tako Ina azabarsu na ratsashi Amma baya iya ko motsa ko yatsansa bare Wani abin
Ga Wani irin duhun da ko a Lokacin da suke shiga gino zinari a Cikin duhun Rami me zurfi da tsayin gaske Bai Kai wannan ba sbd wancan akwai hasken fitila Amma ayau ko wanda zai kunna masa hasken fitila Babu,
Wannan duhun duhu ne da Yan uwansa Dake kwance kabari Kila sunfisa samun rahamar hasken kabari akan wannan dayake Ciki.
Haka ya kwana Babu sauki ko rahamar ubangiji ko daya har gari ya waye sai guraren 10 aka shigo aka Bude dakinsa Wani qazamin dattajo ne da yake a Buge ya zauna ya tayar dashi zaune ya fara Tura masa abincinda ta ringa dawo masa sbd azabar dayake Ciki ta Fi masa abincin Dadi da saukin wucewa a cikinsa.
Ganin hakan me basa abincin ya Saka hannu ya dame tuwo da miyar kaman kunu ya zuba musu ruwa suka sake sakewa ya maqure bakinsa ya dura masa shi gabaki dayansa a bakinsa ya wuce cikinsa.
Yana fita amai ya fara feso masa har jikinsa har qasa take gurin ya lalace da Wani irin qarni da qazantar Aman Amma Babu wanda yazo ya sake dubasa haka Nan ya wuni Cikin aman tareda ruwan qazanta.
Haka ya wuni sai dare aka sake zuwa basa abinci Nan ma Babu Bata lokaci Aka dura masa ya sake feso Wani Aman Cikin azabar ciwon Ciki Mai tsananin azabar daya sakar masa gudawa.
Anan ne aka zo aka daukesa suka wanke masa jikinsa Shima bayan ya wuni Babu wanda ma yasan halinda yake Ciki bayan wari da qazantar sun ma fara bushewa a jikinsa.
Lokacinda suka zaune dashi a bakin Wani fanfafo Cikin qazanta suka fara sheqa masa ruwa qarnin amai Dana jinin rigarsar daya bushe Dana gudawar suka fara Wani mummunan tashi a jikinsa take suka suka rufe hancinsu Suna sake Dan yin baya daga jikinsa suka sheqa masa ruwa kaman Wani Dabba.
Wani irin kukan baqin Ciki da qunci ne ya taso masa Yana rintse Idanuwansa.
Suna gamawa Wani gajeran wandon dinki suka Saka masa suka kaisa dakin hakanan suka kwantar dashi suka tafiyarsu.
Sanyi ne Me karfin gaske suka fara ratsa fatarsa zuwa namansa har zuwa qashinsa suna ratsasa cikeda azaba da qaiqayi Amma ba halin motsawa.
***A daidai wannan lokacin Omar na tareda Dr Aleena wadda sukai tafiya a safiyar zuwa Abuja shi da ita da Ahmed gurin Wani Taron manyan likitocin da zaayi na qasa Wanda tana Cikin manyan baqin likitoci masu Mahimmanci da aka gayyata sbd shi Omar din daya Saka sunanta sbd ta daukaka a qasarsa kaman yanda takeda daukaka a tata qasar akan aikinta.
A lafiyayyan luxury Bangalore dinsa suka sauka Wanda yake tsare da securities da luxuries Tako Ina hankalinsu kwance.
Ahmed bangarensa daban a gidan Dan haka Shima a nasa bangaren ya sauka hankalinsa kwance.
JAMAAL ma dashi a Cikin Manyan likitocin da aka gayyata Dan daga sunan Mum dinsa sai nasa Dan haka Yana Abujan sedai bama tare suka taho ba Dan yaso tahowa da tasa halal din Amma Sam ko muryanta taqi barin ya sake ji daga ranar bare ganin fuskanta Dan ba qaramin fushi da zafi ta dauka dashi ba Dan haka duka yake Cikin dacin zuciya.
Siddeeq ma duk yanda yaso magana da Ashley ta samu Damar fitowa da am din Dan su dauketa kawai su tahowarsu ya kasa samun Damar wannan maganar da ita sbd babbah daya Saka musu mugun Ido musamman Ashley din dan yafi qin yadda da ita akan kowa ma Dan haka ya Saka mata Ido tareda rantsewa akan duk Wanda ya kamata tana waya dashi shi zai aura mata ko waye sbd maganinsu.
Fatmah ma hakan ya fada mata hakama gabaki dayansu ya sakasu dawowa sashensa ya Kuma hadesu a daki daya sbd su duk abinda zasuyi su shirya Babu shegen da zai zauna zaman shiryasu tinda ba Wanda ya hadasu fadan da hassadar tareda qyashin da zage zagen.
Fatmah kusan zaucewa take Neman Yi sbd ganin su Dad Omar da Dad dinta ko ta kan zancensu Basu sake bi ba alaman hukuncin babban yayi musu daidai Dan haka ta sake dagewa da rokon babbah tana Neman tuba da bazata sakeba Amma ko bi ta kan tubanta baibiba.
Ameenatou dai batada ta cewa bayan komawa salihar gaske sbd Cikin kaman Yana jiran asan dashi sai laulayinta ya dauke tsaf Bata Ciwon komai ko Wani amai saima fitowa dayek kokarin farawa sbd tasowa da mararta tafara Yi hakama fushin datake cikinsa akan Jamaal din Bai saukoba ko kadan sbd kunce mata zani a kasuwa ne yayi duk da tasan a gunsa shi ba komai bane tinda bature ne Amma meyasa baima fara fada mata yasan tana dauke da Cikin nasa ba Wanda itama harga Allah taji tana tsananin son Cikinsu yanzu sbd na Arfat Bata hankalinta ta dauki Cikin ya Renu a Cikinta har haihuwansa.
Ashley dai itama taitayinta ta shiga ta Dena waya da kowa se babbah baya gidan dan sanin rantsuwarsa akan duk Wanda ya kamasu Suna waya shi zai aura musu indai auren ya halasta tsakaninsu.
Hafiz da dadah ne ke tausaya musu matiqa musamman Fatmah data kasa Dena Kuka haryanzu gaba daya ta shiga Wani mummunan hali akan abubuwa da yawa Ciki harda Dad Omar data batawa Dan tasan zuciyarsa ta sosu ko yayane da jin abinda tayi hakama iyayenta fushi sukeyi sosai da ita ga Ameenatou da batajin zata sake ganin mutuncinta ga Jamaal din datai abin akansa ma Ashe mahaukaciya ya dauketa ga Babbah da dauren sadakansa gabaki daya ta rasa inda zata Saka kanta a Cikin dakin ma Ashley da Ameenatou Babu me mata magana mugun zama ne sukeyi gashi kowannensu bai Saba da kwanciyar qasa ba idan ma ka Saba sanyin AC kadai da tiles ya dauka zai iya illata rayuwarka Dan haka bame yafewa haka suke shigewa lafiyayyan gadon dakin Anne suyi bacci Cikin Rufa daya.
Hafiz ne da dadah ke Dan rarrashinsu Suna tarairayansu Amma Didi ko gaisuwan Fatmah din Bata amsawa itada Mum Nur Ameenatou ma Mum Nur tayi fushi da ita akan maganar data fadawa Fatmah sbd tsakanin Dad Omar da Ahmed yanzu Yan uwantaka ce data Fi ta jini karfi Dan kuwa kowa a tare ya gansu a tare ya sansu Kuma alaqa ce data Riga ta zama family bazata taba gogewa ba sbd kaf gidan har Ahmed din kowama yayansa da matarsa da Jaden suke amfani a sunansu kaman yanda yanzu duka harsu Hafiz duka an qara jdens a karshen sunayensu so maganar iyaye da rashin daa ba dabia ko hali bane.
Anyi Taron kwana uku din a Abuja an gama a ranar Jamaal ya dawo Lagos tareda Siddeeq Banda su Mum dinsa da ba yanzu zasu dawo ba sai sun kwana biyu sbd wasu manyan kwararrin likitocin da Omar zai hada da Dr Aleena.
Duk Yanda Omar da Aleena din suke ganin yayansu sun girma Basu San sunada sauran lokacinsu ba sosai Saida suka kasance da juna a kwanakin sbd wata lafiyayyan sanyayyan soyayya ce me karfi da kwanciyar hankali suke gudanarwa hankali kwance.
Omar Jaden Bai baro Abujan ba Saida maganar aurensa ta fita duniya tasan matarsa ta biyu wadda ta fita tareda maganar auren ‘yayansu,
Ya gabatar da Dr Aleena second wife dinsa da Kuma son dayake mata itama kaman yanda yakeson matansa duka Dan haka take aka ringa daukansu hotina ana yadawa Kuma kowanne Suna tareda juna kusan ma duk inda zasu hannunsu Yana riqe da juna hotinan ke fita sbd ita dai baturiya ce hakan ba komai bane gareta hakan Shima tinda kusan haihuwansa ne kadai baayi baturen ba Amma Shima turai dinne kawai.
Bayan dawowan Jamaal duk yanda yaso yaga halal dinsa hakan Bai samu ba Dan Babu fuska a gurin babbah Dan haka dole ya fara lallaba babban sbd sai yanzu yake fahimtar zare hannun da Dad Omar yayi yabarsa dashi yasan karfin zuciyar gaske ne dashi saiya masa tasa karfin zuciyar akan son dayakewa ‘yarsa zai gane shi kwata kwata ma baisan meye kunyar sirikin da ake magana ba indai akan a Hanasa halal dinsa ce musamman yanzu datake fama da laulayin babynsa a karo na biyu.
Ganin take taken Hafiz akan son fitar da Yan matan zuwa Wani gurin su samu su Sha iska kansu ya sake ya Saka babbah taka masa Burkin karya kuskura ya shiga Cikin masu karban hukuncin sbd shi kansa me laifin ne sosai a gurinsa sbd duka halinda Ameenatou take Ciki ya sani shine suka Taru suka ci amanarsa aka barsa a iska qaton ga Babbahn mahaukata ko?
Ya kiyayesa sbd Yana laifi daya wlh dashi zai hada ya Basu baqin mamaki.
Hakan ya Saka Hafiz Dan kama kansa sbd yasan babban idan ya Riga ya dauki zafi akan Abu bare yanzu laifi ne akan duka wainda yake ganin sun Saka ‘yarsa taci amanarsa Dan Bai yadda yin kanta bane zugata yake ganin anyi Kuma ba kowane yayi wannan aikin ba bayan Ashley da Siddeeq da Jamaal din kansa harma dashi Hafiz din.
MAMUH
GUDUN ƘADDARA
H U G U M A
Book 02 page 55
Idanunsa suna kan kowanne sashe na sassan nasa,yana nan kaman yadda yake,ba abinda aka sauya ba kuma wani abu daya lalace kamar bai dauki wadannan shekarun baya nan ba.
Duk inda ya gifta ba abinda ke dawo masa sai shekarun samartakarsa, abubuwa da yawa ya dinga tunawa har ya ratsa falonsa yakai ainihin bedroom dinsa.
Yana shiga almu yana ajjiye mop stick din daya gama goge masa tiles din wajen,suka hada idanu da maina din,sai yadan sadda kansa kadan. Abun almu din yana dan bawa maina mamaki,duk ya maidashi wani baqo qarfi da yaji,duk da ko a baya ba sakewa tsakaninsu sai desipline,amma kuma yana tunanin kaman a baqon almu yake kallonsa.
“Ina goumar?” Ya tambayeshi, tambayar data sanyashi daga kai ya kalleshi,don a nasa lissafin maina din bai wani san goumar can can ba
“Sunje niamy…..amma gobe da sassafe jirginsu zai iso da angon yaaya aminata” kai ya jinjina,shuru na wasu ‘yan mintuna ya biyo baya,sai ya gyada kai
“Shikenan jeka,sai da safe”
“Akwai wani abu da kake buqata?” Almu din ya tambayi maina,har qasan zuciyarsa yana jin tausayinsa,duk da baikai wayon haka ba sanda yabar gida amma kuma yana iya tuna kulawa da yake basu,sa’annan a yanzun ya san cewa gagarumin qalubalen dake gaban yaa aliyyun,duk wata kulawa bazai sameta daga iyayensu ba
“Babu” ya amsa masa a taqaice
“Merci” ya sake fadi yana jin dadin yadda almu din ya nuna masa kulawa. A yadda yakeji din baya jin zai buqaci wani abu,nutsuwa kawai yake da buqata da kuma kebe kansa har zuwa safiya. Don haka almun yana fita ya soma zagayawa cikin dakin,yayi ‘yan dube dubensa. Komai yana nan hatta da suturunsa ba abinda aka taba,ya maidasu waje daya ya killace,don a yanzun bazai iya amfani da ko daya daga cikinsu ba.
Kayan jikinsa ya cire ya daura towel ya wuce bandaki. Ya jima yana dumama jikinsa sosai, tunani cunkushe a kwanyarsa. Baisan yaya safiyar gobe zata waye masa ba,baisan da wanne ido da kuma wanne hannu zasuci gaba da tarbarsa,saidai koma meye yana bawa kansa tabbacin juriya da dagewa hadi da jajircewa.
Kayansa da yazo da su ya bude,ya fidda pajamas marasa nauyi ya saka,kwanciya yakesonyi amma bayajin zai iya kwanciyar,don haka ya shimfida abun sallah shima ya kabbara sallah da tarin buqatu dake cikin ransa.
*Tun asuba hayaniyar cikin gidan ta qaru saboda yawan jama’a da kuma hada hadar daurin aure da aka fara yi,wanda duka daurin auren su biyun zai gudana ne a babban masallacin alhj Mohammed mayak’i dake farkon street din nasu.
Tana idar da sallah ko hijabin jikinta bata fidda ba ta koma saman gado,idanunta fal da bacci don a jiya bata samu cikakken bacci ba.
Batasan adadin awannin data shafe tana bacci ba,ta daiji anata knocking sama sama amma bata ko motsa ba,don tasan mutane ne kawai zasu dameta,saidai a yanzun bugun da ake mata yasha banban da wadancan,don yanzun kamar za'a tsinke qofar a shigo,dole ta miqe tana lalubar dankwalinta da ya zame ta sanyawa kanta,sannan ta sauko daga saman gadon ta nufi qofar.
Yasime ne a tsaye,tayi kyau cikin shigar wani arnen farin lace da ya wadatu da ado da duwatsu masu qyalli,kana kallonta basai an gaya maka ba amarya ce, fuskarta ta dauki makeup sosai wadda ta sake bayyana ainihin kyan nan nasu da sukayi gado. Houda na tsaye a gefanta cikin army green shadda da sukayi anko dukkansu 'yammatan amare suka tsara zasu sanya a yau din. Wata harara ta jefa mata
“Wai bacci ma kikey?” Hannu ta sanya tadan dafe kanta
“Da ciwon kai na kwana Yasmin,don Allah karkiyi qorafi” ta fadi tana karya murya. Dariya ta bawa Yasmin din
“Kiyi ki shirya don Allah,kada azo daukan hoto bake a ciki”
“In sha Allah” ta amsa mata,wanda ita kanta tasan ta amsa mata ne kawai,amma sam yau bata sha’awar fita ko nan da can. Harabar gidan gaba daya bata burgeta,ta tabbatar a yau din kusan labarin da zaiyi trending cikin gidan shine labarin dawowar maina. Suna juyawa tana shirin maida qofar ta rufe tanja ta qaraso
“Ama tace na dubaki kin tashi?”
“Na tashi tanja……don Allah tea nakeso me dumi sosai,madara da sugar kadan”
“Tea kawai?” Kanta ta gyada mata tana lumshe fararen idanunta,bakinta babu test kwata kwata,shima tea din zata sha ne kawai maganin yunwa.
Tanja tana fita ta juya ciki ta soma zare kayanta ta fada wanka. Koda ta fito tanja ta aje mata tea din,sai ta zauna ta fara kurba a hankali tana dumama cikinta. A hankali sai tunaninta ya koma daren jiya,wata siririyar faduwar gaba ta ratsa qirjinta,ta maida idanunta ta lumshe tana son kauda surar fuskarsa dake gilma idanunta. Benazeer da batoul ta tuna,wannan ya sanyata ajiye cup din a hankali,ta jawo hijab ta zura ta nufi qofa. Tana gab da fita a dakin wata murya daga can qasan zuciyarta ta jefa mata tambaya
“Idan kinje gurinsun me zakiyi?,zaki hanasu yawo ne bayan gidan cike yake da yara?,kada kiyi abinda mutane ko shi kansa zaiyi tsammanin kin damu da sha’aninsa ne,bake daya ba,akwai dakaru a gabanki da bai isa yace zaya dauki yaran ko ya aiwatar da wani abu ba” ajiyar zuciya me nauyi ta sauke sannan ta dawo da baya jiki a salube,daga tsaye ta dauki tea din ta kurbe,saita koma wajen drawer dinta ta soma duba kayan da zata saka, zuciyarta da tunaninta haka kawai ya raja’a akan yaran.
Tun asuba yayi alwala ya kuma fita sallar asuba kamar yadda kowanne namiji dake gidan yakeyi tun gabanin barinsa gida,har kuma yanzun babu abinda ya sauya. Yana qoqarin fita daga makeken gate din gidan sukayi kacibus da aba adan hanzarce,da alama shima yaso ya makara ne. Idanu suka hada da aba din,sai ya janye idonsa tamkar ma baisan mainan ba,ya kuma qara taku ya wuceshi a sanda maina ke yunqurin yi masa magana. Ajiyar zuciya me sanyi ya sauke yana lumshe ido hadi da budeshi,wannan abun idan aba yana masa shi yana sanyashi jin tamkar zai mutu. Ba haka ya saba masa ba,a shekarun baya kafin komai ya faru idan sukayi kacibus irin hakan da hannu yake masa nuni da ya matso,idan ya matso din kuma sukan wuce masallaci tare da aba din kafada da kafada,a yanzu da yake ganin akasin hakan sai yakejin kamar zuciyarsa zata tsinke daga qirjinsa,bazai iya jurar wannan halin ko in kula na aba ba. A baya yaci gaba da bibiyarsa har suka isa masallacin,sanda aba ke qoqarin kafa sahu cikin zafin nama ya tsaya daga gefansa,ya kuma daidaita sahunsa dana aba din. Yayi zaton zaiyi wani motsi amma sai yaga ko daga kai ya dubeshi baiyi ba,tamkar ma baisan dashi suka hada sahu tare ba.
Suna idar da sallar aba din yadan ja gaba ya fita a sahun,sannan ya zauna sosai ya fara azkar din daya zame masa.jiki duk safiya muddin yana da lafiya,idan kuma baya dan jin dadi yana komawa gida yayi cikin falonsa balcony ko bedroom dinsa.
Daidaikun mutane da sukasan maina sai suka dinga matsowa suna gaisawa dashi tare da tambayarsa yaushe ya dawo qasar,saidai ya danyi murmushi yace musu
“Jiya” yadda suka dinga masa barka ya alamta masa lallai sunyi zaton karatu ya tafi. A hankali a hankali yana gaisawa dasu har zuwa sanda suka kammala,ya dan juya idonsa kadan ya saci kallon aba. Yadda yake tun dazun har yanzu a haka yake a zaune,yaja numfashi sosai,sannan ya miqe cikin mazantaka ya taka izuwa garesa.
A gabansa ya zube gwiwoyinsa,muryarsa cike da girmamawa da kuma rusunawa ya furta
“Barka da asuba aba” idan carbin dake hannunsa ya amsa shi shima haka,sai yaci gaba da jan tasbaharsa baiko motsa ba bare maina ya sanya ran ya jishi. Sake maimaita gaisuwar yayi,wanda yana direta aba din ya yunqura ya miqe yana durfafar qofa,baiyi qasa a gwiwa ba ya take masa baya,saidai kafin ya cimmasa har ya sanya slippers dinsa masu tsananin taushi ya soma barin farfajiyar masallacin.
Dab da zai fita ya cimmasa,ya sake taresa karyar da wuya dama murya gaba daya
“Aba…….na roqeka don……”
“Bakaji abinda na gaya maka ba jiya?,kai wanne irin mahaukacin yaro ne?, meye alaqata da kai da zaka dinga bibiyata haka?,ni bani da wani d’a me kamanceceniya dakai,ka fita daga harkata tun kafin na saka hukuma su kamamin kai” yayi maganar a fusace yana nunashi da yatsa,sannan ya kewayeshi yana wuceshi bayan yaja dogon tsaki. Sosai jikin maina yayi sanyi,abinda yake gani a idanun aba din me girma ne,anya zaici gaba da tunkarar aba?,anya ba bibi bace kadai tsaninsa kaman yadda oncle issoufou ya gaya masa?.
Cikin qarfin hali yaci gaba da takawa cikin gidan. Koda yakai bai koma sassansa ba sai ya zarce sashen ama. Can dinma mutanen daya samu a sassanta wadanda suka tattashi sallah dukka basu koma ba binsa suka dinga yi da kallon yaushe gamo?,ya gaisa da wadanda zai iya gaisawa dasu,ya tambayi bilki me aikinta ta gaya masa yanzun ta shiga daki.
Sau uku yana knocking sannan ya murda qofar,bakinsa dauke da sallama,qasan zuciyarsa cike fal da addu'a. Da ita ya fara tozali,tana zaune saman tattausan abun sallarta dinnan,jikinta sanye da ustazah hijab da skirt dukkansu kala me haske. Tsananin tsafta da gayunta ya santa kusan komai nata me hasken kala ne,sai dai daiku masu duhun kala. A nutse ya qaraso cikin dakin,ya kuma yiwa kansa mazauni a qasan dandagaryar turkey carfet din dake malale a dakin wanda ya qarawa dakin kyau da kuma tsari.
Hannayenta a sama tana addu'a,sai shima ya buda nasa tafukan hannayen,sanda ta kammala suka shafa a tare,sannan ta waiwayo suka hada idanu.
Kwarjinin nan nata yana nan,gaba daya fuskarta ta cika da hasken ibada sanin kima da martabar kai. Wani lokaci su uncle abdulhakeem kan bata lokaci kan cecekucen kwarjinin da yayo gadonsa yayi,amma basusan tsakanin hamid da hamdiyya waye yafi wani kwarjini ba?.
Sai data gama zuba masa dukka dafin kwarjinin idanunta sannan ta janye daga kallonsa. Zuciyarta na hira a kansa ita kadai. Mainan nata ya girma,ya zama cikakken mutum wanda ta tabbatar akwai maganganu masu yawa da labarai cikin tafiyarsa da kuma dawowarsa,saman kowacce fuska akwai labari......cikin kuma kowanne littafi nan ma tasan akwai labari,amma a yanzu bata jin zata bashi wannan qofar ko damar haka a kurkusa. Kaman yasan niyyan tashi ta bashi waje takeyi sai yayi caraf da dukka hannayenta ya kuma hanata miqewar,koda ta daga kai ta kalleshi sai ta tsinci hawaye fal idanunsa. Kuka a idanun aliyyu?,abinda zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba gani ba,tun yana qaraminsa kuka abune me wuya a wajensa bare kuma sanda ya mallaki hankalin kansa,yana da tsananin fushi kafiya da zuciya,wannan ya sanya ko yara sa'anninsa basu fiya takalar fada dashi ba,idan kuwa kayi gangancin yin hakan kaine zakasha qasa
“Don martabar fiyayyen halitta ama kada kiyimin haka,aba haka yakemin tun jiya,kema haka zakiyimin ama?,idan duk duniya sun gaza fahimtata ama na dauka ke zaki riga kowa fahimtata,ke zaki fara sauke fukafukan jin qanki a kaina ama?,ban tafi don wata manufa ba,banyi nesa daku saboda na rainaku ba…..hasalima nayi nesa daku ne saboda kunyar keta maganarku……saboda kunyar na aikata abinda ya kamata ace ya zama sirri ne tsakanina da ita saidai nayi ta yadda ya zai fita,na tafi ne saboda bansan da idanun da zan kalleku ba,bansan da bakin da zanyi muku bayani ba……ama……. wallahi wallahi wallahi ban tafi da nufin na tafi daga gareku kenan gaba daya ba…….na tafi ne da niyyar idan kun huce zan dawo……a raina ban taba sakawa zan tafi nayi koda wata guda ba…….sai kuma gashi komai ya sauya……ina biye daku ama……ina biye da duk wani motsinku ama…….ban yanke daga shiga rayuwar sultana tare da sanin hakinda take ciki ba ama……amma kuma saidai a cikin tarko nake……ina cikin wani dauri da muddin na bayyana a gareku rayuwata na cikin hadarin da bani da gatan da zai fiddani…. Lokacin kuma da nake tunanin na zama free……ina da ‘yanci sai yayi dai dai da lokacin da zan cika BURIN ABA…..MAFARKIN ABA…..burin dana tabbata a duk sanda na bayyana a gabanki babu shi kema zaki qalubalanceni BABBAN LIKITAN ZUCIYA kuma DAN KASUWA CIKAKKE…..Na hadu da jarrabawar da na tabbatar barinku ne sila……na kuma hadu da lalurar da afuwarku da kuma yafiyarku ne kawai zai bani maganinta……” Hannu ta daga masa tana yin qasa da kanta,batason yaga zallar rauni da karaya daya zubawa zuciyarta,batason yaga tausayin daya lullube qirjinta,irin tausayin da dukka uwa keji akan d’anta komai girman laifi ko kuskurensa,saboda kasantuwar zuciyar mahaifiya ta banbanta da zukatan mutane gaba daya,koda kuwa ita wannan uwar wata halitta ce daban bata dan adam ba……
“Banason naji komai daya faru dakai,koda zanjin zanji ne a tare a kuma lokaci guda da mahaifinka,kaje ka nema yarda mutum ukunnan…….sannan ka dawo gareni” sai ta zame hannunta tana miqewa.
Shima bai zauna din ba sai ya miqe yayi tsaye yana kallonta tana barin dakin
“Kiyimin alfarmar amsa gaisuwata ama…..koda iya ita kadai na roqeki” har ya fidda rai don takawa take tana barin dakin,kamar kuma ba zata amsa ba,dab da zata fita din tace masa
“Nayi maka” cikin dubunnan nauyikan dake qirjinsa yaji kaman an cire daya,ya fesar da iska me nauyin gaske da ya fusgota daga cikin cikinsa yana aza tafin hannunsa saman fuskarsa wani farinciki yana dan ratsashi,sa’annan yana jin qwarin gwiwarsa ya sake qaruwa. Sai daya ji ya nutsu sannan ya soma fita a dakin,cikin takunsa me cike da qasaita,saidai kuma a yau din a sanyaye yake takawar.
Bangaren bibi ya nufata kai tsaye,shikam a yau yakeson gamawa da bibi din,don dama bai azata a ma'aunin matsala ba,ya duba agogo dab da zai shiga sashen,ya kwasarwa drama dinta awa daya kacal,don yanason ya koma bangarensa ya sake runtsawa koda na awa daya ne sannan ya shirya ya fito,don yanason ayi daurin auren 'yan uwansa dashi.
KWANKWASON JIMINA
TSUTSAR NAMA
AMEENATOU
GUDUN KADDARA
Tor littafi ya fara zuwa inda muke jira….Allah ya saka muku ameen
Tanks
Masha Allah
Amma pls yaushe za mu samu continuation
bata yi bane
OK tnks