𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣
…….Shiru kawai yay yana kallon takarda da key ɗin motar da sakatariyarsa ta kawo masa na tsawon lokaci, kafin ya furzar da huci mai kauri ya tashi zaune sosai da ga kwanciyar da yay a kujerar office ɗin nasa. Wayarsa mai ƙyau da ɗaukar ido ya ɗauka. Har yay dailing number da akai saving da _Yaya Isma’il_ sai kuma ya katse yana ɗan girgiza kansa. Dan ya san halinsa, wani lokacin ba gane abubuwa yake ba birkitaccen mutum ne. Wata number ya sake lalubowa yay dialing, ring biyu aka ɗauka.
“Uncle You.. Good Afternoon”.
Aka faɗa daga can, muryarsa a sauƙaƙe ya amsa da “Afternoon dear! How are you?”.
“Am good Uncle”.
“Haka ake so. Lulu ta dawo ne?”.
“Yes Uncle tun ma ɗazun. Sai dai tanata masifa wai Uncle Smart ya barta a airport. Amma Deen ya ce ta masa ihu ne a gaban mutane kuma bai mata komai ba kadai santa. Yanzu kuma Daddy ya goya da bayanta wai zata walaƙanta shi ta koreshi. Uncle ALLAH ni bana so sumasa haka, shi ɗin mutum ne nutsatstse”.
Wani ɗan murmushin takaici yayi da gyada kansa kamar yana a gabansa. “Karka damu Son! bazan bari su aikata hakan ba insha ALLAHU. Kuma zai dawo aikinsa”.
Sosai yaron ya shiga ihun murna daga can. Shi kuma ya katse wayar yana mai jin takaicin hali irin na ɗan uwansa. Yanda yake training rayuwar Mawaddat na ɓata masa rai. A rayuwa ko ɗa namiji ne bazakace komai ya nema sai ya samu ba duk arziƙinka da matsayinka. Balle mace da wataran aure zatayi ta koma ƙarƙashin ikon wani. Wanin da ba lallai shi ya iya ɗaukar waɗan nan ɗabi’un nata marasa ƙyau ba. Da wannan ɓacin ran yabar office ranar. Kai tsaye gidansa ya nufa dake anguwar ta Hotoro GRA shima. Sai dai ba street ɗin su ɗaya da gidan yayan nasa ba. Da gudu ƙyawawan yaransa guda uku masu kama da shi sukazo tarbarsa. Murmushi yayi cike da jin daɗi, gaba ɗaya ya haɗasu ya rungume a jikinsa bayan sun gaidashi. Yana ƙoƙarin miƙewa da ƙaramin Deen da sukaje ɗaukar Lulu airport mai wayon tsiya a hannunsa idonsa ya sauka akan matarsa. Ƙyakykyawar mace ƴar duma-duma. Murmushi ya sakar mata kamar yanda take masa itama, ya miƙa mata hannu alamar tazo itama. A hankali ta ƙaraso ta shige jikinsa, rungumeta yay da sumbatar goshinta kamar yanda ya saba. Ko’a jikin yaran dan sun saba ganin hakan ga iyayensu, basa aikata wani abu dazai lalata musu tarbiyyar yara, amma su tarbi juna yayin da wani yay ɗan nesa da gida kona yini guda ne sun nunama yaransu hakan ba komai bane face ƙauna, kuma ya halatta miji yayma matarsa, idan sunga hakan ko’a wani waje ba haramun bane ba. Shiyyasa suma yaran suke kallon hakan a normal ne.
Da ƙyar ya samu ya gudarma Deen dake bashi labarin faɗan aunty Lulu a airport. Bayan yay wanka falon ya dawo ya zauna cikinsu yana shan fruit salad. Matarsa Saleeha da kowa ke kira da Aunty a family ɗin ta kallesa cikin damuwa da sauƙaƙa harshe. “Abul Mahsin kamar kana cikin damuwa? Wani abun ya sake faruwa ne a office ɗin?”.
Ƙaramin tsaki yaja da ɗan girgiza kansa. Kamar bazaice komai ba sai kuma ya numfasa. “Mawaddat! Halin yarinyar nan nacimun rai matuƙa Sweetheart. Kullum maimakon abubuwan su dinga sauƙi tana hankali amma sake jagulewa yake. Abinda yafi ɓatan rai Yaya. Shi sam nunawa yake kamar ma komai yana tafiya daidai ne a rayuwar yarinyar. Safiyya ina tsoron UBANGIJI ya tuhumemu akan amanar da baiwar ALLAHr nan ta tafi tabar mana fa…”
“Tabbas hakane, to amma ya zakayi tunda Yaya yana sama da kai ne. Ita kuma ɗabi’un sun riga sun shigeta tankwarata abune mafi wahala duk da ma kana iya bakin ƙoƙarinka tun bata kai haka ba. Amma babu abinda ya canja”.
“A wannan karon ina son ya canja kota ƙarfi Saliha. Dan gaskiya na gaji da gani, bana son yarinyar nan ta kuma fi haka gagara…”
“Tankwarawar ta ƙarfi kam akwai damuwa, dan shi icce tun yana ɗanye ake tankwarashi. Idan ya bushe akace za’ayi zai iya karyewa. Sai dai ni inada shawara. A yanda Deen ya bani labarin abinda ya faru tsakaninta da drivern nan nasan zasu ce zasu koresa ne, inaga karka bari hakan ta faru, inma da dama ya zama driver nata ita kaɗai, dan shi naga ba mutum ne mai wasa ba, ba kuma zai ɗauki halinta ba”.
A hankali ya sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ya furta, “Nagode miki dan tunaninmu yazo ɗaya. Sai dai magana ta gaskiya bamma san yanda zan tunkari yaron ba. Kedai kin san a yanda na samosa ai, aikin nan kuma yana yinsa ne saboda tsare mutuncinsa bawai irin sauran drivers nada bane da take takawa yanda take so. Sannan Aliyu yanada zuciya fiye da yanda kike tsammani da hasashe bar ganinsa hak shiru-shiru baya son magana”.
“Duk ɗan halak dole ya kasance mai kishin kansa Abul Mahsin. Sannan wannan itace cikar kamalar duk wani ɗan adam na ƙwarai. Karka ƙasƙantar da kanka ga kowa ga komai saboda talauci, ka kasance mai tsaftatacciyar zuciya a baɗini da zahiri, ka kuma zama jarumi a neman na kanka koda duk jama’a na kallon hakan da faɗuwa. Ni nasan baka kawosa yay wannan aikin da ƙasƙanci ba, sai dan wani dalilinka da kuma kare mutuncinsa daga taɓarɓarewar abubuwan da ba’asan mafari ba a rayuwarsa. Kamar yanda kuka samu mahaifinsa a farko kai da Ahmad yanzu ma ku sake samunsa insha ALLAHU zai dawo ya cigaba har ALLAH shima ya kawo masa iyakar komai na jarabawarsa”.
“Shike nan in sha ALLAHU zan gwada nagani. Ita kuma zuwa anjima zanje gidan na sameta”.
“Hakan yayi, amma Please smile”. Ta faɗa tana kwatantawa da hannunta a kan baki. Hararta yay yana sakin murmushin…..
∆••••∆ ★ ∆••••∆
Washe gari ma baiyi yunƙurin zuwa aiki ba, sai ma tunanin neman wata mafitar da ya tashi da shi. Kamar yanda ya saba bayan dawowa sallar asubahi ya shiga sashen mahaifinsu domin gaishesa duk da tare suka fita massalaci suka kuma dawo. Ƙyaƙyƙyawan dattijon mutum mai cike da tarin nutsuwa. Da ga gashin kansa har zuwa na gemu fari ne fat. Duk da tsufansa ya bayyana a kallo guda zaka tabbatar da zamanin ƙuruciya ansha ƙyau. Duk da ya ɗan ɗago ya dubesa a lokacin da yake shigowa bai ajiye littafin dake a hannunsa ba. Sai ma ɗan turɓune fuska da ya sake yi. Tsahon mintuna uku baida alamar kulashi, har sai da wasu samari biyu suka shigo, abin mamaki sai ga murmushi ya mamaye fuskar tashi, ya ajiye littafin cike da kulawa idonsa akan samarin dake gaishesa bayan sun ma Uncle Smart kallo ɗaya a gatsine sun ɗauke kai. Oho baima san sunai ba, dan basu isa masa a ido cikin ido ba.
“Abba Barka da safiya”.
Suka faɗa kusan a tare. Cike da kulawa yake jinjina musu kansa. Ya amsa da “Har an shirya fita kasuwar? Ƴan albarka”.
“Eh Abba”.
Suka bashi amsa suna miƙewa. Albarka ya shiga saka musu, suko tunda suka amsa sau ɗaya ma basu sake ba. Har zasu fice ya dakatar da su. Cikin ƴar damuwa yake kallonsu. “Nabeel yau kam da ban takuraku ba da kun bama iyayenku kuɗin cefane. Na tashi banda ko nera a jikina gashi babu hanyar samuwarsu garan a yau”.
A turɓune wanda aka kira da Nabeel ke dubansa. Bakinsa a sama ya ce, “Abba kafa san abubuwan sai a hankali. Kuɗin cefanen gidan nan inba kaiba kuma wazai iya. Sannan jiya fa sai da kasa na baka dubu biyu”.
“Nima ai sai da na bashi dubu ɗaya”.
Ɗayan ya amshe da sauri shima rai ɓace. Ɗan murmushi Abban yayi, yayinda Uncle Smart kejin wani irin raɗaɗin zantukansu ga mahaifinsu akan abinda bai taka kara ya karya ba. Mahaifinsu jarumin ubane da ya tsaya a kansu da ƙare ƙarfinsa wajen gina rayuwarsu. Amma yau sun zama wani abu kowa najin ƙyashin taimaka masa. Ɗari biyar-biyar suka ajiye masa saɓanin abinda ya tambaya suka fice rai ɓace. Gaba ɗaya sai yaji jikinsa ya ƙara sanyi, cikin ƙarfin hali ya fara gaida Abban dake sake ƙoƙarin ɗaukar littafinsa bayan ya kwashe dubu ɗayan da suka ajiye masa. Maimakon amsa masa gaisuwar a zafafe ya ce, “Shima wannan aikin sun korekan?”.
Kasa amsawa yayi ya ƙara ƙasa da kansa zuciyarsa na ƙuna. Ba’a kan ƙaddararsa ba, ba kuma akan abinda mahaifinsa ke tuhumarsa ba, sai akan damuwa da halin da mahaifin nasu ke ciki….
“Wai halan bada Ali nake magana ba?!”.
Ya faɗa cikin fusata.
“Kayi haƙuri Abba dama….”
“Dama mi? Mi kake son faɗamin? To wlhy bari kaji a wannan karon bazan ɗauka iskancinka ba. Bari ma na faɗa maka gaskiya in har maganar banzarka ce da ka saba to a wannan karon ka shirya barmun gida, dan bazan iya cigaba da wahala da kai ba bayan wadda nayi kana yaro. Na ciyar da kai abinci, na tufatar da kai sutura, na sakaka a makaranta islamiyya data boko har matakin digiri na biyu sannan na cigaba da wahala da kai. Ga kanenka nan na bayan baya sun tsaya da ƙafafunsu harda masu aure amma kai ban daina cidaka abinci ba, wannan wace irin rayuwa ce. To ba asiri ba a wannan karon ko kukar bulukiya aka sauke a kanka bazan ɗauka ba na gaji da shashancin ka, tashi ka ficemin daga nan na baka zuwa dare wlhy ka tsara mai yuwuwa sakarai kawai cima zaune”.
Idanunsa da suka kaɗa sukai jazur ya ɗago kaɗan ya subesa. “Kayi haƙuri Abba ALLAH ya huci zuciyarka, dan ALLAH ka gafarce ni”.
Banza ya masa bai sake tankawa ba. Yasan minene shiru a wajen mahaifin nasu. Dan haka ya miƙe ransa a matuƙar ƙuntace ya fice. Har ya nufi hanyar sashensu na samari ya fasa. Ƙirjinsa zafi yake masa. Ji yake kamar ya saki kuka amma bazai iyaba saboda taurin zuciyar tsiyarsa. Sosai mutane ke kai kawo a cikin layin nasu. A halin da yake ciki baya buƙatar yin magana da kowa, dan haka yay ƙoƙarin juyawa zai koma ciki. Daga motar da tun fitowarsa idonsa ya sauka a kanta amma ya kauda kai aka danno masa horn. Ƙin juyawa yay har sai da aka sake na biyu da ambaton sunansa. Cak ya tsaya amma bai juyo ba har Uncle Yousuf da abokinsa Ahmad suka ƙaraso garesa.
“Kayi haƙuri”.
Kalmar data tilastashi juyowa da ga bakin Uncle Yousuf……….✍️
_Alhmdullah, mungode da haƙurinku. Bari muga a fara ko kaɗan-kaɗan kafin na murmure. Mungode sosai da addu’oin ku🙏._
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣
………Hannu ya basu batare da ya yarda ya kallesu ba. Uncle Yousuf yay murmushi da amsar hannun sukai musabaha bayan ya gaisa da Ahamd dake ƴar dariya saboda harar da Uncle Smart ɗin ke masa ƙasa-ƙasa.
“Idan ban takura da yawa ba ina son muyi magana Please Smart Mawashi”.
Karan farko ya ɗan ɗago idanunsa da har yanzu suke da damuwa ya dubi Uncle Yousuf mai maganar. Kamar zaiyi magana sai kuma yayi shiru. Uncle Yousuf ya sake murmusawa da faɗin, “Please”.
Bashi da yanda ya iya dole ya amince masa, sai dai maimakon cikin motarsa da ya buƙata suje anan cikin soron gidansu suka zauna saman bench. Shiru na wasu mintuna kafin Uncle Yousuf ya nisa. “Jiya na dawo na samu takarda da key ɗin mota a hanun sakatariyata Aliyu, sai dai ban gamsu da bayanin dana gani a rubuce ba shiyyasa nace Ahmad ya rakoni nazo da kaina”. Ya ƙare maganar idonsa a kansa alamar son jin amsa.
“Na ajiye aikin ne kawai”.
Ya faɗa cikin dakewarsa.
“Ko miyasa?”.
Ahmad ya tambaya cikin kafesa da idanu.
Kansa ya jinjina yana ɗan furzar da iska, sai kuma ya dubu Uncle Yousuf maimakon Ahmad da yay tambayar. “Saboda bazan iya ba Alhaji. Ni mutum ne da ba komai zuciyata ke iya ɗauka ba duk da na kasance talaka mai nema.”
“Haka ake so duk mutum na ƙwarai ya kasance Aliyu Hydar. Amma har yanzu baka faɗa mana dalilin ba?”.
Murmushi ya saki mai ciwo a karo na farko. Ya ɗan dubi Uncle Yousuf ɗin sai kuma ya ɗauke kai. “Miye amfanin maimaita abinda bashi da muhimmanci koya wuce Alhaji. Kawai na ajiye shikenan ya wuce. Nasan insha ALLAHU zaku sami wanda ya fini, ni kuma zan tara gaba maybe abincina ba’a nan yake ba”.
“Nasan bazaka juraba kamar na baya da suka shuɗe domin Kanada banbanci da su. Sai dai irinka na jima ina fata ni kuma, dan kai kaɗaine zaka iya da ita har ma ka tankwarata. Har yanzu nasan baka san ni wanene ba Aliyu Hydar, sai dai ka sani ban nema kamin wannan aikin ba dan kana buƙatar aikin da kuɗi zai shigo maka. Tun randa na ganka wajen abokina yayan abokinka Ahmad naji a raina ka cancanta zama wani ɓangare da zai jagoranci haska wata fitila ta rayuwarta. Ita ɗin a fanɗare take, tabbas a haka ta tashi shiyyasa tanƙwarata yayma kowa wahala a cikinmu. Ada kallon komai muke a bigire na ƙuruciya da tunanin wata rana zata daina, sai dai ranar har yanzu taƙi tazo, bamu san kuma ranar da zata zo ba, ko kuma tazo ne ta wuce batare da mun farga ba oho?. Nasan kana da ƙanni mata maybe ma harda yayu, kasan irin zafin da nakeji a raina koda a kwatance ka kwatanta da ace sune, miyasa bazaka gane ba ne….?”
Yanda ya ƙare maganar a raunane cikin sigar tambaya yasa Uncle Smart fesar da iska mai nauyi. A ɗan zafafe batare daya dubesu ba yace, “In dai har ku da kuka haifeta kun gagara tanƙwarata ni kuma taya kuke tunanin iyawa? Mahaifinta fa na raye, hakama mahaifiyarta, sannan gaku ku ƴan uwanta, Alhaji Please kayi haƙuri bazan iya ba fa. Bana son raini, bana iya jurarsa ga kowa. Bana son wulaƙanci ko ƙasƙanci duk da kasancewata talaka mai nema. Ina ganin kimarka dan ALLAH karka bari mu shiga wata hanya daba ita ta dace mukai ba dan alkairi ya haɗamu kuma bazan taɓa na manta da kai ba, dan kamun abinda mutane da yawa basu minba na alkairi ka gaida gida”.
Yana gama faɗa ya miƙe. Dakatar da shi Ahmad yayi, kamar bazai tsaya ba sai kuma ya dakata tare da juyowa. Miƙewa shima Uncle Yousuf ɗin yayi yana ɗan murmushi. Hannu ya kai ya dafa kafaɗarsa, “Shike nan na fahimceka kuma nagode sosai. Ina son mutum irinka mai tsayawa akan ra’ayinsa da riƙe mutuncinsa. Zan jima inajin raɗaɗin rabuwa da kai Aliyu. Amma dan ALLAH ina roƙon alfarmar kazo office ko zuwa gobe ne domin amsar hakkinka, kuma bana son kace da ni a’a”.
Baki ya buɗe zai yi magana Ahmad ya dakatar da shi. “Dan ALLAH karkace a’a Smart, ban sanka da musu ba karka fara akan Yaya Yousuf, sannan kayi nazari akan roƙon da yay maka, nasan kanada damar taimakons…..”.
Hararar da ya ɗan ballama Ahmad ɗin ce ta sashi yin ƙaramar dariya batare da ya ƙarasa ba. Ɗauke idanunsa yay da faɗin, “Shike nan insha ALLAHU idan na samu lokaci zanje, amma kai ma kasan kawai dai dan ta Yaya boss ne wlhy”.
“Na sani Mawashi. Yaya boss kuma na godiya da wannan karamci”. Bai ce komai ba, sai murmushi da Uncle Yousuf dake saurarensu yayi. Har cikin rai ɗabi’un yaron birgesa sukeyi matuƙa. Yana son ganin mutum mai nutsuwa musamman matashi kamar haka. Ba irin matasan yanzu da shegen rawar kai yayma mafi yawansu katutu ba…
Har mota ya musu rakiya. Bayan wucewarsu sai yaji ya kasa komawa cikin gidansu dan baisan da wane irin harshe zaima Ammah bayani akan sake rasa wannan aikin ba shima, duk da dai jikinsa yay ɗan sanyi da kalaman Ahmad na ƙarshe, amma dai bai yanke hukunci ba na sake amsar aikin har yanzu. Sai dai in ya tuno bayanin Abba ya kanji faɗuwar gaba. Tabbas yasan wanene Abbansu, sam baya magana biyu. Mutum ne tsayayye da idan yace e to e ɗinne da har ransa. Idan kuma yace a’a to a’a ɗin ce fa. Da ƙafa yabar cikin anguwar tasu, rashin abunyi da sanin ina zai dosa ya sashi miƙewa a titi yay ta tafiyarsa kawai. Yayi tafiya mai nisa da bai san ina yake jefa ƙafa da ɗaukewa ba ya fahimci kamar binsa akeyi a baya. Tsamm yayi na tsarguwa tare da tsayawa, sai dai abin mamaki babu alamar wani tare da shi a ƙafa, wanda ke a kan mashina ma da napep babu alama, hakama na mota. Dakewa yay ya cigaba da tafiyar, still dai ya sake jin tabbas akwai mai binsan. Yanzu kam bai juyo ba sai ya yanke titin ya shiga cikin wani layi, ya ɗan yi nisa da layin sosai ya samu rumfar wasu masu kayan kafinta ya ɗan dakata cikin dabara kamar mai gyara igiyar takalmi. Ta cikin mirror da aka jingine ya hango wasu samari biyu, sai dai suna ɗan waskewa cikin ɓadda kama. Hakan ya ɗan bashi mamaki, dan shi dai a rayuwa duk da yana da tsatstsauran ra’ayi bashi da abokin faɗa. Cigaba yay da tafiyar dan son gane iya gudun ruwansu badan yasan sirrikan layukan inda yake ba. Sai da sukaje ƙarshen layin sosai ya fahimci akwai matsala, ya ɗan ji wani abu a ransa amma sai ya dake, wata hanyar da yake ƙyautata zaton zata ɓillesa da titi ya bi, sai dai yana shan kwanar tsukin wajen suka sami nasarar rufesa ruf ata gaba da bayansa. Ɗaya bayan ɗaya ya bisu da kallo har ya sauke akan napep ɗin da aka faka a gabansa. Cikin dakewa da ambaton sunan ALLAH ya ce, “Ku kuma fa?”.
“Zaka sani amma ba’a nan ba”.
Ɗaya ya bashi amsa cikin gatse da nuna masa bindiga dake soke a ƙugunsa. Bindiga bata kasance abar wasa ga kowa ba. Duk ƙarfinka da taurin kai a duk inda mai ita ya kasance shike zama a saman ƙarfin ikon ka. Dan haka ya shiga napep ɗin zuciyarsa na saƙa masa abubuwa masu yawa game da mutanen. Biyun da suka dinga binsa ne kawai suka shiga gefe-da-gefensa, mai napep yaja suka fice daga layin, sai da suka fita gaba ɗaya wanda ke gefen haggunsa ya jefa masa wani ƙyalle a fuska, da sauri na kusa da shi ya kama ya ɗaure masa idanu yayinda wanda ya fara jefa ƙyallen ya ɗora masa bindiga a gefen ciki ta yanda bai isa musawa ba. Duk da ya sake firgita haka ya dake a zahirance, a baɗini kuwa yana mai ambaton sunan ALLAH……
Tofa, su kuma waɗan nan daga ina?. Wayyo Uncle Smart ɗinmu😫😢
∆••••∆ ★ ∆••••∆
Tun daga main falour na gidan kana iya jiyo tashin sautin kiɗan dake fitowa da ga ɗakinta, duk da kiɗane mai taushi na mawaƙiya Shakira yanda ta ƙure voluen yasa ake iya jiyowa. Tun safe babu wanda zai ce ya ganta yau a gidan har zuwa yanzu da agogo ke nuna ƙarfe takwas da wasu mintuna. Mafi yawan yaran rai a ɓace suke fitowa daga ɗakunan su dan sautin kiɗan data saka ya takurasu da hanasu barcin safen. Hatta da ƙananun Suhaib da Imran da fita makaranta kan hakanasu barcin safen ji suke ta takura musu, musamman Imran dake son ƙarasa Assagment ɗinsa amma ya gagara fahimtar komai. Kaf ɗinsu sun gama hallara a dining, sai dai fuskar kowanne a turɓune da takaici. A haka Daddy da Mommy suka fito suka samesu, a kallo ɗaya zaka fahimci itama Momy ranta a ɓace yake, sai dai shi Daddy kam ko’a jikinsa. Yaran ma na gaidashi bai wani saurarensu ba hankalinsa nakan kiran Tabawa mai aiki. Da ɗan gudu-gudu ta fito a kitchen hannunta riƙe da ƙaramin ludayi da alama girki takeyi.
“Babyna fa?”.
Ya faɗa kai tsaye yana nuna upstairs. Itama upstairs ɗin ta kalla, cikin sake rissinawa tace, “Barci takeyi Alhaji, tace zuwa ƙarfe tara da rabi na tadata”.
“Shi kuma wancan kiɗan da ga ina?”.
“Itace ta kunna”.
Nunin ta tafi kawai ya mata batare da ya sake cewa komai ba. Mommy da tai kicin-kicin da fuska ya kalla, sai kuma yabi sauran yaran nasa da kallo. Hafiz dake ƙoƙarin kai shayi bakinsa wanda a haihuwa shike bima Lulu ne ya ce, “Humm Daddy yanzu bazakace komai ba kenan?”.
“Akan me?”.
“Aunty Lu. Ai ko kafiri ba kowa ke iya saka kiɗa ya kwanta da shi ba. Kuma ina da tabbacin ko sallar asuba batayi b…..”
“Kai ban san shashanci da ƙazafin banza, wai Hafiz ita ɗin sa’arka ce? Kuma kai ubanwa yace maka batai sallar ba”.
“Ai ba sai wani ya faɗa masa ba abinda kowa ya sani ne. Ni ban san wane irin makahon so kakema Mawaddat ba a gidan nan, kuma ka sani wannan ba gata bane kashe mata rayuwa kakeyi matsayinta na mace. Da haka kowace yarinya ake rainonta a gidansu da baka gammu haka ka aura ba matsayin iyayensu Alhaji. Dan ALLAH ya kake so nayi da raina akan Mawaddat ne?”.
Wani banzan kallo ya galla mata ita da yaran baki ɗaya yana cika da batsewa, sanin yanzu zasuyi sama ya sata miƙewa tabar dining area ɗin zuciyarta na ƙuna da raɗaɗi. Ta rasa mike damun mijin nata akan babbar ƴarsu mace, yana nuna mata ƙazamar rayuwa a matsayin soyayya, iya bakin ƙoƙarinta tana yi akan Mawaddat amma abubuwa sake taɓarɓarewa sukeyi. A hankali hawaye masu raɗaɗi suka silalo mata saman kumatu………✍️
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣
……..A can falo kam tashin Mommy dai-dai da shigowar Uncle Yousuf, da murna yaran suka tarbesa. Sai dai ganinsa kamar rai ɓace yasa jikinsu sanyi. Abba da shima idonsa ke kansa ya baro dining ɗin ya nufosa. Kusa da shi ya zauna idanunsa a kansa ɗan uwansa, yana son ɗan ƙanin nasa namiji ɗaya tilo da ya rage masa a duniya.
“Anya lafiya kake cika kana batsewa haka?”. Ya faɗa cikin kulawa da dafa kafaɗarsa. A hankali yace, “Ba komai. Sai kuma ya kai dubansa ga sashen Lulu. “Wannan kiɗan fa?”. Shima Daddyn kallon saman yayi, sai kuma yay ɗan murmushi da faɗin “Kaima ka sani sai dai ƴar gidanka ai”.
Komai Uncle Yousuf bai sake cewa ba, sai rumtse idanu da yay cikin takaicin yayan nasa. Kusan mintuna biyu kafin ya buɗe, “Yaya mika yanke akan yaron dana kawo?”.
Murmushi Daddy yay mai bayyana haƙwara. Ya ɗan bigi kafaɗarsa cikin sigar zolaya ya ce, “C-mon magajin baba saki fuskar mana, ni idan kana wannan cikar sai naga kamar baba ne ya dawo fa”.
Baki Uncle Yousuf ya tura masa kamar mai shirin yin shagwaɓe fuska. Sai kuma ya kauda kansa saboda murmushin da ke son kufce masa. Sam baya iya dogon fushi da ɗan uwan nasa. Shima Daddyn murmushi ya sake saki da faɗin, “Yauwa ko kai fa. Yanzu kamun bayani yanda zan gane. Wane yaro kake magana a kai?”.
A taƙaice ya ce, “Driver”.
“Okay ni babu abinda na yanke. Dan Babyn ka har yanzu tace tana buƙatarsa ai”.
“Shi kuma baya buƙatarmu dan ya ajiye aiki”.
“Wannan ra’ayinsa ne ai. Idan itama ta haƙura sai a nema mata wani ba damuwa bane”.
Wani shegen takaici ne ya sake kume Uncle Yousuf. Shi bai san wane irin mutum bane yayansa. Sam bai damu da damuwar kowa ba sai kansa da su ahalinsa. Kai kawai ya jinjina yana miƙewa. Daddy dake binsa da kallo ya ce, “Badai wucewa ba?”.
“Yaya to mizan zauna nayi kuma. Ina son dai ka sake tunani a wannan gaɓar. Domin duk a yanda muke kallon rayuwa da ɗaukarta yaya watarana sai ta tsere mana ta ɗakko wasunmu a madadinmu. Zata iya yuwuwa kuma ta ɗakko waɗanda muke kallo ba kowa ba su kasance a saman tamu damar”.
“Hakane Auta, sai dai ban san dalilin wannan gugar zanar ba”.
Murmushi Uncle Yousuf yay mai ciwo. “Nasan ka sani Yaya, duk da ni ba gugar zana nake maka ba. Sai dai akan Mawaddat kana rumtse idanunka da kunnuwanka domin ƙin amsar gaskiya”. Daga haka ya nufi part ɗin nata. Yanda yake haɗa ɗan steps ɗin shiga sashen da bibbiyu zai baka tabbacin ransa a ɓace yake. Sai da ya rumtse ido lokacin daya ɗaura hannunsa kan handle ɗin ƙofar ɗakin nata. Batare da ya yarda ya kalla ɓangaren da gadonta yake ba ya nufi kayan kiɗan ya kashe. Kafin cikin daka tsawa ya ambaci sunanta. A firgice ta tashi tana mai yaye ƙaton lallausan bargon data jibgama kanta. Gaba ɗaya gashin kanta madaidaici a tsaho ya wani hargitse, sanye take da wando da riga na pyjamas farare tas masu santsi da ƙyalli. Kasancewar sun mata bujin-bujin yasa basu bayyana mata surar jiki ba. Ya ɗan samu nutsuwar ganinta da kayan mutunci, dan haka ya kalleta cikin ido babu wasa a tattare da shi ya ce, “Kinyi sallah?”.
Tana son Uncle Yousuf matuƙa dan shima yana sonta da mata gata. Sai dai kuma baya wasa akan tarbiyyarta da gyara lamarinta shiyyasa take tsoronsa idan ya birkice, dan yasha kwasa mata mari mai gigitarwa. Akwai wani lokaci da ƙawaye suka yaudareta suka sakata dawowa gida a wani yanayi da ga club da ya ɗauketa da wani mahaukacin mari sai da ta yini jinta bai dawo ba. Tuni kuma ta watsakke daga makuwar da tayi…..
“I say kinyi salla?!!”.
Ya sake maimaitawa a tsawace fiye da farko. Daburcewa tai ta ɗaga masa kai ta kuma girgiza. Sai kuma ta sauka da gudu a gadon kamar wata ƙaramar yarinya ta nufi toilet ɗin ta. A cikin mintunan da basu gaza biyu ba ta fito fuska da ƙafafu jiƙe da ruwa wai tayi alwala. Abin salla da Tabawa ke faman ajiya a ma’ajiyarsa kamar na ado dan ba sallar take ba sai randa taso ta ɗauka ta shimfiɗa. Akan kayan barcin ta zumbula hijjabin da shima dai baida banbanci da kayan decorations na gida gareta. Uncle Yousuf na daga inda yake tsaye har yanzu cikin ƙunar rai. Fara sallar da bata da fasali balle makama da gamata ba’a ƙulla mintuna biyu cikakku ba. Hankalin Uncle Yousuf ya ƙara tashi. Dan yau ne karan farko da ya fahimci Mawaddat bata iya ko salla a yanda MANZON ALLAH ya koyar ba. “Innalillahi wa’inna ilaihiraji’un” ya shiga maimaitawa jikinsa na tsuma. Baima san sanda ya kai zaune jagwab cikin kujerar kusa da shi ba. Yanzu nan kamar Mawaddat mai shekara ɗai-ɗai har ashirin da huɗu tana cikin ta biyar, mai karatun matsayin cikakkiyar lauya da duk wanda ta tsayama a shari’a zai iya alfahari da itace babu wata ƙyaƙyƙyawar alaƙa tsakaninta da UBANGIJINTA a ɓangaren bauta masa irin haka. Wane irin sakaci sukan sukai da shagala akan al’amarin yarinyar nan har haka?…..
“Uncle You! please kayi haƙuri kar kai fushi da ni”.
Kalamanta cikin damuwa suka katse masa tunani. Tuni ta rarrafo gabansa ma hijjab ɗin na harɗeta batare da ya sani ba. Idanu kawai ya zuba mata dan shi kam tausayi ma take bashi wlhy. Shi mutum ne mai zafi amma kuma yana da saurin sauka da kuma sauƙin kai shiyyasa yaran ɗan uwan nasa ke sonsa, dan ya taso ne kamar duk shi ya raine su. A hankali ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi. Muryarshi a rissine bakamar ɗazun ba ya ce, “Mawaddatan-wa’rahmah!”.
A hankali ta ce, “Yes Uncle”.
“Mi kikayi haka?”.
“Uncle salla mana da kace”.
“Bani nace ba ALLAH ne yace ayi kuma ba haka akeyi ba. Mawaddat wannan ranar ita nake gudun zuwa gareki shiyyasa nake zaneki idan kikaƙi zama Islamiyya a shekarun baya kafin abar ƙasar nan da ke, shiyyasa kuma na dage a nema miki malamin da zai koyar da ke addini bayan Yaya ya maidaki can. Yanzu ace kamarki, ɗiyan musulmi hausawa ƴar ƙasar Nigeria a arewa amma baki iya salla ba? Innalillahi wa’inna ilaihiraji’un. Mawaddat da duk mi kike yi ke kuwa a duniyar nan haka? Mi kikaima kanki tanadi na tunkarar UBANGIJI da har kikejin ƙwarin gwiwar baje kolinki a duniya da abinda ke cikinta kawai? Anya kin yarda zaki mutu kuwa? Za ki kuma kwanta kabari? Za kuma a tasheki? Za’a kuma miki hisabi sannan ki ƙarɓi sakamakon makomarki?. Makomar da gida biyune kacal dole kuma ka tsinta kanka a ɗaya wuta ko aljanna………”
“Uncle Please kabar zancen mutuwan nan mana. Badai sallan bane kuma nayi. Kaga inama da zuwa court zuwa ten ga shi har nine na neman wucewa.”
“Wato shi zancen sallan baida muhimmanci ko?”.
“Noo Uncle You! Bance ba fa. Kawai dai ni…..”
Sai kuma tai shiru. Kansa kawai ya girgiza dan y fahimci ba irin wannan zaman na kai tsaye Mawaddat ke buƙata ba. Yana buƙatar yin nazari akan al’amurinta kafin ya nemo mafita mai ɓullewa. Da hannu yay mata nunin ta tashi da faɗin, “Okay jeki shirya”.
“Yawwa Sweet Papa na!!!”.
Ta faɗa da ihu tana miƙewa. Kansa kawai ya girgiza yana mai karanto mata addu’ar shiriya wajen UBANGIJI kamar yanda ya saba akoda yaushe ya tashi ya fice dan bata damar yin shirin….
∆•••∆ ★ ∆•••∆
Da ƙyar ya iya buɗe idanunsa da sukai masa tsananin nauyi ya fara bin inda yake da kallo. Falo ne babba mai ɗauke da kaya na alfarma. Sai garadan samari guda biyu dake tsaye a kansa da alama sune suka ajiyesa a wajen. Akan mutumin dake zaune cikin kujera mai zaman mutum ɗaya ya tsaida idanun nasa. Shima kallonsa yake yi. Fuska ya ƙara tsukewa tare da kauda kansa, babu alamar tsoro tattare da shi ya ce, “Su waye ku? Mi nakeyi anan?”.
A karo na farko mutumin yay murmushi har ana iya jin sautinsa. Kansa ya jinjina da faɗin, “Abinda duk aka faɗamin game da kai naga fiye ma da hakan. Sanin ni wanene gareka baida amfani. Abinda ya kawoka nan kuwa shine aiki. Idan kaso zaka iya ɗaukarsa a business ɗin da zaka ƙaru kaima, idan kuma kai tunanin bijirewa ko cigaba da wannan zafin kan naka to komai zai iya faruwa. Sunanka shine *_Aliyu M. Idris Mawashi._* Mata huɗu ne a gidanku ƴaƴa talatin da biyu. Mahaifiyarka itace ta farko a wajen babanka, ku biyar ta haifa ɗaya ya rasu. Kai kaɗaine namiji biyu sunyi aure kanada kanne mata biyu yanzu haka Maryam da Asma’u. Yanzu haka suna a ajin karshe a sakadire, islamiyya suna ajin hadda. Babbar yayarka na auren Alhaji Abubakar Azare itace amaryarsa. Bata sonshi mahaifinku ya haɗasu, yaranta biyu duk maza. Kanwarka dake bimaka tana auren abokinka Sa’id Ibrahim, yarinyarta ɗaya da ciki. Kana cikin matsanancin rayuwa sosai akan al’amuranka daba sai nayi zaman lissafasu ba ka sansu kaima”.
“Daka sanni har kamar haka, amfanin mi zai maka?”. Uncle Smart ya faɗa cikin zafin rai.
Ƙaramar dariya mutumin yayi yana wani ɗage kafaɗa. “Amfani masu yawa kuwa, ciki harda abinda zuciyarka bata kawo maka ba. Dan duk wanda na buƙaci alaƙa da shi dole ne ya amince min. Inba haka ba zai fuskanci abinda babu shi a lissafin rayuwarsa. Idan kuma ya amince lafiya zamuyi mu gama cikin mutunta juna na ƙaru ya ƙaru”.
“Sai kuma gashi ni ba’aimun barazana?”.
“Ba barazana nake makaba nima. Ina faɗa maka abinda zan iya yine koda a yanzu ne da kake gabana. Aliyu Mawashi! Ko nace Smart Mawashi ni bana faɗar abinda bazan yi ba. Idan na faɗa maka zanyi to na gama shirya yanda zanyi ɗin ne. Ka kwantar da hankalinka aikin da zakamun bamai wahala bane ba, sannan kaima zaka fita a ƙangin damuwar rashin abunyi da kake a ciki, maybe ma ka tsallake ƙasar nan insha ALLAHU a wannan karon ka samu cikar burinka. Mahaifiyarka ta samu kwanciyar hankali da samun salamar hantara daga kishiyoyi da miji, rayuwar ƙannenka ta inganta kamar yanda kake fata. Mahaifinka ya cire zargin da yake maka da fifita ƴan uwanka a samanka duk da bawata tsiya suma suke tsinana masa ba…..”
“Waye kai?”………✍️
*_Ku ƙara haƙuri dani dan ALLAH. Idan na ɓalle typing har sai kunce ya isa haka in sha ALLAHU🙏😩_*
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 9️⃣
……..Dariya sosai Alhajin ya kwashe da shi. “Karka damu da sanin ni wanene saboda nasan kai waye? Sanin aikin da zakai min kawai ne yafi muhimmanci. Dan na sanka fiye da yanda na faɗa maka a yanzu. Kaɗan na tsinkulo a sanin danai maka kawai. Gidan daka ajiye aiki nake so ka koma ka cigaba da min aiki. Duk wata zan baka albashin naira dubu hamsin bayan albashin da su suke baka dubu ashirin”. Ya ajiye masa wani envelope gabansa da cigaba da faɗin, “Wannan shine kundin ayyukan da zakamin a gidan Alhaji Isma’il Jiƙamshi. Zan iya baka dama ta kwana ɗaya kaje kayi tunani, sai dai ka sani ko’a cikin ɗakinka idanuna a kanka suke, dan haka da zuciyarka kawai nake buƙatar kayi nazari. A duk sanda nake buƙatar magana da kai zan nemeka tanan” ya ajiye masa waya akan envelope ɗin daya ajiye gabansa. “A yanzu bana buƙatar cewarka anan, kaje kayi nazarin na barka lafiya. Ku maidashi”. Ya ƙare maganar da duban yaransa cikin bada umarni
Da wani irin kallo mai nuna tsananin zafin zuciya Uncle Smart ya bisa. Sai dai da alama ran ƴan maza ya ɓaci dan ya kasa furata komai…..
Kamar yanda Alhajin ya bada umarni sun maidoshi har kan titin anguwarsu. Kasancewar magrib yayi a gurguje ya ƙarasa gida domin watsama jikinsa da yay nauyi ruwa. Ya samu wasu daga cikin samarin ƙannensa sun dawo gidan. Wanda ya samu a waje suka gaishesa. Da hannu ya amsa musu kawai ya shige ɗakinsa. Shi mutum ne mai tsafta sosai da ƙwanƙonin tsiya, dan haka ganin ɗakin a yanda ya barsa ya sashi jan tsuki yana ɗan dafe kansa dake masa ciwo. Har yanzu abinda suka shaƙa masa bai gama sakin masa jiki ba. A karan farko ya laluba aljihunsa neman wayarsa, cikin sa’a ya jita. Ƙanwarsa Maryam ya kira, suna zaune a falo suna karatun Alkur’ani kiran ya shigo, cike da zumuɗi Asma’u da wayar ke’a gefenta ta ce, “Lah Yaya ne”. Kallonta Ammi da Maryam ɗin duk sukayi, ita kuma ta ɗaga da sallama. A hankali ya amsa mata cikin muryarshin nan a dake da wasu ke fassarawa da girman kai da suke kallonsa da shi saboda shiru-shirunsa, batare daya bata damar cewa wani abu ba ya cigaba da faɗin, “Zan samu ruwan zafi a wajenku?”.
“Eh Yaya”.
Ta amsa masa cike da girmamawa. Tana ajiye wayar Maryam tace, “Ya dawo ne?”. Kai ta ɗaga mata da faɗin, “Ya dawo, cayay na kai masa ruwan zafi, inaga wanka zaiyi”. A hankali Ammi ta sauke ajiyar zuciya, sai dai batace da su komai ba ta cigaba da laziminta. Tun safe hankalinsu ke’a tashe, dan bai shiga gidan gaishesu ba kamar yanda ya saba. Da farko Ammi tayi zaton koya fita wani uziri ne, sai da ta shiga gaida Abba ya yanka mata baƙar magana son ransa, kamar yanda ta saba yin shiru akan ƴaƴanta idan yana faɗa haka yanzu ma ta haɗiye, sai da ya gama ta bashi haƙuri, sai dai furucinsa akan zai bar masa gida ya matuƙar tayar mata hankali, har ta aika Maryam kira mata shi ko yana ɗaki amma suka samu baya nan ɗakin ma a buɗe, neman number sa ta shiga yi amma sai ba’a ɗaga ba, daga ƙarshe ma ta daina samunsa. Da wannan damuwar ta yini yau ita dasu Asma’un.
Koda Asma’u takai masa ruwan zafin sai da ta gyaro masa toilet sannan ya shiga, ɗakin ta shiga kimtsa masa shima. Kafin ya fito harta kammala ta fice. Kasancewar anyi sallar magriba yay tashi a ɗaki sannan ya fice massalaci yin isha’i. Bayan an idar gidan ya sake komawa. Abba bai shigoba, dan haka ya wuce cikin gidan. Kamar yanda ya saba sai da yabi duk ɗakunan matan gidan ya gaidasu. Da ɗakin Aunty Amarya ya fara. Mace ce mai yawan fara’a da son mutane, sai dai kuma bata da yawan magana itama. Duk da zai iya sa’anni da ita hakan bai hanashi girmamata saboda yanda take girmama Ammi a gidan itama kamar ba kishiya ba. Ya gaidata cikin mutuntawa, ta amsa masa da kulawa. Yaranta dake sabgogin gabansu a falon tun shigowarsa duk suka nutsu dama. Duk sun gaidashi, yayinda ƙaramar tazo jikinsa tana kawo masa ƙarar ɗan uwanta dake bima babbar ɗakin nasu cewar ya karya mata pencil ɗinta tana homework. Da sauri yaron mai suna Abbas ya ce, “Yayanmu ƙarya take ita ta karya abunta a makaranta suna faɗa da Ameer. Kuka ta saka itama tana faɗin, “Ƙaryane Yaya shine”. Hannu ya ɗaga musu duk sukai shiru. Aunty Amarya tace, “Ai inba ubansu kaci ba Yayansu ba barin kunnen mutane ya huta zasuyi ba. Tun ɗazu suke rikicin nan ni harna gaji ma da magana”.
Faɗa yama yaran cikin sigar nasiha, yace da safe kafin su wuce makaranta Anisan tazo ɗakinsa ta amshi sabon pencil. Da ga haka ya fito zuwa ɗakin Umma. Itace ta biyu a gidan, amma itace mai manyan ƴaƴa a sakamakon rashin samun haihuwa da Ammah bataiba da wuri, kusan duk sunyi aure kuma. Sai dai tanada sauran ƴammata biyu a yanzu haka da samari biyu da basuyi aure ba. Ta amsa masa a ɗan fisge, bai damuba dan hakan ba sabon abu bane a garesa. Nusaiba autarta dake gefenta zaune tana cin abinci ta gaidashi itama. Amsa mata yayi yana miƙewa. Dakatar da shi Umman tayi da faɗin, “Yau lafiya kuwa bamu ganka da safe ba?”.
Ɗan murmushin ƙarfin hali yay mata da faɗin. “Ba komai Umma na fitane da safe sosai wani uziri”.
“Uhhm to yayi”. Ta faɗa a taƙaice.
Iska ya ɗan furzar da ga bakinsa kawai ya miƙe yana ficewa. Ɗakin Mama ya nufa, mace ta uku a gidan, sai dai ya samu tana sashen Abba dan itace da girki yau. Mansur ƙaninsa ɗanta na huɗu kawai ya samu a falon da yarinyar ƙanwarsu (jikar gidan) tana barci a kujera. Gaishesa Mansur ɗin yayi yana wani nannoƙe kai na rashin kunya, sai dai babu damar yi dan suna tsoronsa a gidan ba kamar sauran yayunsu maza da suke iyama rashin kunya ba. Amsa masa yayi yana kallon askin kansa na rashin tarbiyya.
“Idan na wayi gari na ganka da wannan askin bisa kai kayi kuka da kanka”. Daga haka ya fice. Baki Mansur ya tura gaba yana ƙunƙuni da yarfa hannuwa. Sai dai babu damar yi da ƙarfi.
Ammah na zaune su Maryam a gefensa suna cin abinci da kallo film ya shiga da sallama. A tare suka amsa masa da gaishesa cikin girmamawa. Ya amsa musu da kulawa yana kaiwa zaune. Ammah ya gaida da bata haƙurin rashin shigowarsa da safe. Dai-dai nan Maryam ta ajiye masa abinci da fure weter. Ɗakinsu suka shige da abincin dan sun san akwai magana a bakin Ammah. Suna shigewa kuwa ta dubesa da ɗauke kai ta ce, “Lafiya ka fita tunda safe?”.
Samun kansa yay da faɗin, “Lafiya lau Ammah naje wajen aiki ne”.
A hankali ta sauke numfashi. “Nasan ba son aikin nan kake ba Hydar. Sai dai mai haƙuri yakan dafa dutse har yasha romonsa. Kafi kowa sanin yanda gidan nan ya koma yanzu, miyasa bazaka sakama kanka haƙuri da mutane ba ka karɓi rayuwa a duk yanda tazo maka. Kowane bawa daka gani akwai irin tashi ƙaddarar, amsarta da haƙuri kuma shine mizanin imani. Zuwa yanzu yakamata ace kun bar mahaifinku ya huta dako ciyar da kune, shekarunsa yaja yana buƙatar hutu na rayuwa dana jiki. Yasha matuƙar ɗawainiya da ku tun kuna ƙanana har girmanku, bai tauye kowannenku ga ilimi ba da ci da sha da kula da lafiyarku har girmanku. A yanzu kune ya kamata ace kun rungumesa shima tare da ƙannenku da suka rage a gabanmu, dan wataran kune zaku maye gurbinmu garesu a yayin da ƙasa ta rufe idanunmu”.
Gaba ɗaya jikinsa ya ƙarayin sanyi da nasihar mahaifiyar tasa. Idanunsa sun kada sunyi ja, cikin gyaɗa kai da tausasa harshe ya ce, “Inasha ALLAHU Ammah zaki sameni fiye da yanda kike buƙata. Kuyita haƙuri damu kuma kuci gaba da mana addu’a”.
“Addu’a kullum cikin yimuku muke babu fashi”.
Sun cigaba da hira da mahaifiyarsa da ƙanensa da suka fito ya nuna musu assagment har zuwa ƙarfe tara da kusan rabi sannan ya fito. Ɗakinsa ya koma dan yasan yanzu Abba ya riga ya kwanta. Sai da yay shafa’i da wutiri ya samu kwantawa, abinda ya faru a yinin ya shiga dawo masa dalla-dalla. Envelope ɗin nan ya ɗakko ya fara dubawa. Takarda ce kawai a cikinsa ɗauke da rubutu mai ɗan tsaho, abubuwan da aka rubuta ɗin ya matuƙar bashi mamaki harma ya rasa wane kalar tunani zaiyi a kai. Shi dai har yanzu babu abinda zai iya ƙaraswa akan Jiƙamshi family na ƙwarai ko akasinsa. In ma akwai abinda zai iya faɗa to maybe akan wannan ballagazar yarinyar ne ta jiya, siririn tsaki yaja saboda tunota da yayi. Takardar ya yasar gefe ya kwanta yana mai lumshe idanunsa dake cike da barci……
Washe gari da abubuwa da yawa ya tashi a cikin rai. Mafi girman jagorantar ƙarfin gwiwar sa nasihar Ammah, sai kuma wani dalili nasa akan mutumin jiya da son sanin manufarsa ta haƙiƙa, dan yasan in ma bai amshi aikin ba zai iya saka wani yay masa, shiko duk da bai gama sanin suwaye Uncle Yousuf ɗin ba sai yaji bazai iya sakacin barin ƙofar da za’a cuta musu ba har sai yasan gaskiya a kansu. ƙarfe bakwai da kwata a gidan Uncle Yousuf ɗin yay masa. Yana zaune a gate wajen maigadinsu suna ƴar hira kasancewar mutumin Dattijo ne nutsatstse mai aikinsu ta kawo breakfast. Cikin girmamawa ta gaidashi shi da maigadin. Hannu kawai ya ɗaga mata ya ɗauke kansa. Harta juya zata koma maigadi ya tsayar da ita da tambayar Alhaji ya fito ne?.
“A’a nadai ji aunty na batun tadoshi an kirata a waya wannan masifaffiyar aunty Lu suke kiranta ko ta gidan Alhaji Babba bata da lafiy…..”
Bata gama rufe baki ba sai gashi ya fito kamar a ɗan rikice. Tun daga nesa ya ƙwalama maigadi kiran ya buɗe masa gate. Miƙewa maigadin yay da hanzarinsa, hakan yasa Uncle Smart ɗin shima miƙewar ya nufesa. Ganin yanda ya daburce yama kasa tantance motar da ya ɗakkoma key yay masa sallama. Juyowa yay ya ɗan kallesa, har ya ɗauke kai sai kuma ya sake jiyowa.
“Alhamdullah” ya faɗa yana miƙo masa key ɗin batare daya tuna cewa yanzu fa ba ƙarƙashin su yake ba. Babu musu ya amsa key ɗin, dannawa yay motar tai ƙara, dan haka ya nufeta. Sai da ya dai-daita ta sannan, yana batun fitowa ya buɗe masa yaga ya buɗe gaban motar ya shiga yana faɗin, “Yi sauri Please da alama abun babbane, dan duk ciwon Mawaddat da zai iya saka Aunty Kareema ruɗewa irin haka ba ƙarami bane ba”.
Gudu kawai ya ƙara batare da yace komai ba dan ba fahimtar akan wa ake maganar yay ba shi dai. Bawani nisane tsakaninsu ba, dan layinne kawai ba ɗaya ba………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 🔟
……..Ko parking bai gama yi da ƙyau ba Uncle Yousuf ɗin ya fice, ba’a rufe mintuna biyar cikakku ba sai gashi ya fito ɗauke da Lulu yaran gidan biye da shi cikin tashin hankali. Shi ya buɗe masa motar, sai lokacin ma yasan itace. Wani iri yaji a ransa musamman tuna abinda akace game da ita a takardar jiya da Alhajin nan ya bashi. Da wannan tunanin yaja motar suka fice a gidan. Kai tsaye wani babban p-hospital mai suna *_SHIRA’S HOSPITAL_* suka nufa. Yanda aka tarbesu zai tabbatar maka da an san da su. Har yay zamansa a mota sai kuma ya fita yabi bayansu, dai-dai nan suma ƴan gidansu da suka biyo bayan su motarsu ta iso cikin asibitin.
Duk wani kai kawo da ake a kanta shi dai nashi ido ne. Yayinda acan ƙasan zuciyarsa yaketa tufƙa da warwara akan abubuwa da dama. Musamman akan abinda ya dawo da shi aiki cikin wannan family ɗin a karo na biyu. Tabbas ya amshi aiki, sai dai kuma bada manufar wanda ya bashi aikin ba. Dan ko kaɗan baiji wani kurari daga gargaɗinsa sun tsoratashi ba. Hasalima shi wanda ya bashi aikin da yasan shi ɗin wanene maybe dabai bashi ɗin ba. Amma zaiyi, dan in bai amsa ba zai bama wani da zai iya masa yanda yake so… Ringing ɗin wayarsa ne ya katse masa tunani, ya ciro wayar daga aljihu yana miƙewa ya fito. Sallama yay bayan yakai wayar kunnensa, daga haka bai sake magana ba sai saurare. Bayan ya katse kiran ya cire wayar a kunnensa yana furzar da iska kaɗan. Cike da iya nazari yake bin farfajiyar asibitin da kallo a kaikaice, can idonsa ya sauka akan abinda yake nema. Basarwa yay ya share na wasu mintuna, kafin ya nufi fita gate ɗin a nutse. Dai-dai inda almajirai ke zaman bara ya dakata, naira ɗari biyu dake aljihunsa ya ciro ya saka a kwanon barar wani gurgun almajiri dake kan katako mai tayu, almajirin ya shiga jera masa addu’a. Yana ƙoƙarin juyawa matashin saurayin dake gefensa kaɗan yazo ta gefensa suka bangaji juna, kallon juna sukai kamar cikin jin haushi. Sai dai shi saurayin yay saurin faɗin, “Yi haƙuri abokina ban lura bane ba”. Kai kawai ya kaɗa masa yabar wajen batare daya tanka ba.
Maimakon komawa cikin asibitin sai ya samu waje a harabar ya zauna abinsa, can kusan mintuna uku yay ƙoƙarin ciro wayarsa a aljihu sai yaji takardar da saurayin nan ya saƙala masa a aljihu sanda sukai karo batare da ya lura ba. Zarota yay ya warware cike da mamaki, sai kuma ya shiga ɗan waige-waige amma babu alamar saurayin ko wani da zai ce hankalinsa a kansa yake.
_“Ni kamar iska nake, a duk lokacin data kaɗa sai anji sautinta a dukkan ƙofofin gashi na jiki. Idan kuma nai shirin zuwa waje matsayin guguwa tarwatsa komai da kowa na gari nake hatta ruwan kogi baya tsira da ga mamayata. Ka kula, in ba hakaba ni na ƙulleka a cikin ƙullina Aliyu Hydar Mawashi”_.
Wani irin tashi tsigar jikinsa ta farayi na ɓacin rai. A take zuciyarsa ta fara kaikawo da sauri-sauri cikin ƙirjinsa. Takardar ya ninke ya maida aljihu, yana batun tashi waya ta sake yin ringing a jikinsa. Wayar dai da Alhaji nan ne ya bashi jiya, yana kuma ƙyautata zaton takardar nan ma da ga garesa take duk da ya kirashi ne ɗazun a wayarsa. Shi sam yama manta da wayar. Cirota yayi daga aljihun, kamar bazai ɗaga ba sai kuma miya tuna ya ɗaga tana gab da tsinkewa ya kai kunne. Baiyi magana ba daga can ma akai shiru, ganin ana neman shafe minti guda ya katse shirun da faɗin, “Inada abinyi fa Malam”.
Ƙaramar dariya akai daga can tare da faɗin, “Wannan girman kan naka da gizago kesani ƙara jin ka dace da buƙatar aikina Smart Mawashi. Mutanena sun sanar min ka koma aiki, weldone daka kasance mai biyayya irin haka da saurin gane abu….”
“Na koma ne badan kurarinka ko farfagandarka ba! Ko a tunaninka sakawa ana bibiyata da kawomin wasu banzayen saƙwanni a takarda ko kiran wayata zaisa nayi abinda kake so?”.
Ya faɗa cikin katseshi murya a dake. Dariya akayi da ga can, Alhaji ya ce, “Muɗauka haka ɗinne to. Sai dai ka sani ni samaniya ne mai rufe rufin kowanne gida da daji. Abinda kaga ya faru har ya kawoku asibiti yau ka ɗauka shine signing na contract ɗinmu da kai. Ya rage naka ka fara aiwatar da ayyukanka yanda ya dace ko kai kuskuren nunamin zafin kai na cigaba da nuna maka sauran kalolina. Dan a duk inda Jiƙamshi family suke ni nan da kake ji da gani zagaye nake da su har a cikin ɗakin kwanansu, har ma da kai kanka a yanzu….”
Baki ya buɗe zai yi magana ƙittt aka yanke wayar, da sauri ya cirota daga kunnensa, ƙoƙarin kiran layin ya shigayi sai dai yaƙi shiga, ya koma wajen massage danya tura sai ya gama babu app na massage a wayar kwata-kwata. Cikin tsarguwa ya ɗan fara dube-dube, sai dai babu alamar wani da hankalinsa ke a kansa a eriya ɗin wajen gaba ɗaya. Wayarsa ya ciro ya kwashe number da zummar yin kira sai dai kuma taƙi shiga, wadda aka kirashi a farko ya gwada kira itama taƙi shiga. Yay ɗan shiru ransa a dagule, tunanin kiran wani abokinsa yay da zummar masa tracing layukan sai kuma ya fasa saboda tuna maganar mutumin. (A duk inda kake idanuna a kanka suke koda a cikin ɗakin barcinka ne). Fasawa yay ya maida wayar aljihu yana jin zuciyarsa ta masa nauyi da tunani kala daban-daban.
Gaba ɗaya wannan yinin haka ahalin Jiƙamshi gaba ɗaya suka yisa a asibitin tare da shi. Bai yi yinƙurin komai akan son sanin abinda ke damunta ba. Yana dai biye da motsin kowa har zuwa azhar da Uncle Yousuf ya buƙaci ya kaishi gida zai ɗan watsa ruwa. Sai da suka hau hanya yake tambayarsa ya mai jiki. Cikin damuwa Uncle Yousuf ya ɗan furzar da nannauyar ajiyar zuciya tare da dafe kansa ya ce, “Da sauƙi za’ace, dan tunda muka zo sai yanzu ne aka samu kanta har barci ya ɗauketa. Shiyyasa nake son a yau mubar ƙasar nan dan ban taɓa ganin Muwaddat a cikin halin ciwo mai tsananin irin wannan ba. Ban san mi yarinyar ke son maida kanta ba, ban taɓa tunanin rashin jinta ya kai haka ba sai yau, yanzu doctor ya ɗan fara min bayanin wai shaye-shaye ne ke son jawo mata matsala, ban san wane irin rayuwa yarinyar nan take son kai kantaba kuma. Amma duk laifin Yaya ne da ke nuna mata ƙazamin gatan da shi a gurinshi yake ɗauka so ne…” yaja tsaki mai nuna tsananin ƙunar da zuciyarsa ke masa. Da gani kasan yana jin zafi ne a ransa har yake furta abinda bai kamata ya furta a gaban driver kamarsa ba. Sai dai shi kansa ya matuƙar girgiza dajin kalaman Uncle Yousuf ɗin. A ransa faɗi yake (No wander idanunta sam babu kunya da mutunci a cikinsu ashe ƴar shaye-shaye ce) wani irin tsanarta yaji ta sake ɗarsuwa a ransa, ashe bayan ballagazanci harda shaye-shaye. Da ƙyar ya iya furta ma Uncle Yousuf cewar “ALLAH dai ya bata lafiya Alhaji. Sai dai addu’a, a wannan zamanin yara mata da yawa suna cikin wannan mummunar ɗabi’ar ta shaye-shaye, wasu samari ke ɗorasu wasu ƙawaye, wasu matsin rayuwa maimakon suyi tawakkali da haƙuri su maida al’amarin su ga UBANGIJI sai su zaɓi wannan hanyar mara ɓillewa. Wasu ko tsabar gata ne da jin daɗin duniya ke kwasarsu. Sai dai fatan ALLAH ya shiryesu ya kare wanda kuma basu fara ba dan abin tashin hankalin harda matan aure ma yanzu”.
Cikin tsananin damuwa Uncle Yousuf yace, “ALLAH ka shiryar mana da su. Kayi mana maganin duk wasu azzalumai dake safarar mugayen abubuwan nan zuwa ƙasashenmu suna ɓata mana yara”.
“Amin ya rabbi”.
Ya amsa masa dai-dai yana shiga layin gidan Uncle Yousuf ɗin…..
★A ranar bai samu damar zaman yin magana da Uncle Yousuf kan batun dawowarsa aiki ba. Dan yana shiga yay wanka sake fitowa yay suka koma asibitin. Zuwa yanzu kam ta samu barci kamar yanda yaji ƴan uwan na faɗama Uncle Yousuf. Sai a lokacin ya samu damar gaisawa da Daddy daya iso yanzu da ga Abuja da Mommy ya jajanta musu. Cikin ƙarfin hali Daddy ya ce, “Kamar yaron nan daka kawo ne kace kuma ya ajiye aiki jiya Yousuf?”.
Kai tsaye Uncle Yousuf ɗin ya ce, “Shine Yaya. Sai dai banyi magana da shi ba dai bayan wadda nace maka nayi, amma inaga ya dawo aikinsa ne”.
Daddy ya ɗan ja numfashi da faɗin, “Dama Baby batace bata buƙatarsa ba ai. Amma mu jira har ALLAH ya bata lafiya sai muji ta bakinta dai”.
“Uhum”
Kawai Uncle Yousuf yace. Mommy ma dai dake jinsu batace komai ba sai ma ɗauke kanta tai gefe dan haushin mijin nata akan ƴarsu da zata iya rantsuwa da ƙazamar soyayyar da yake matane duk ya zama silar komai na halin da take ciki a yanzu. Duk da dai basu ji komai da ga bayanin likita ba amma yanzu zasuje garesa suji ɗin. Su duka ukun suka nufi office ɗin Doctor Khalil Shira………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣1️⃣
……..Nagartaccen likita nutsatstse da ya san makamar aikinsa. Cikin girmamawa ya gaida Mommy da Daddy, Uncle Yousuf kuma ya bashi hannu sukai musabaha dan zasu iya zama sa’anni. Kusan mintuna uku ya nisa yana mai gyara gilashin idanunsa da ɗagowa ya ɗan kallesu. “A ɗazun mun ɗan fara magana da Yousuf wani hanzari ya katseni, shiyyasa na buƙaci ganinku ku duka saboda muhimmancin abinda zan faɗa game da lafiyar Muwaddat”.
“Doctor ALLAH dai yasa ba wani mummunan ciwo bane, idan kasan akwai matsala dan ALLAH ka barmu mu wuce da ita ƙetare kar sai al’amarin ya ƙwace azo ana wallahi tallahi zuciyarmu bazata iya ɗauka ba”.
“Ka kwantar da hankalinka Alhaji, bawai matsalar zamanta anan ko fitar da ita zuwa ƙasar waje ne damuwar ba. Sanadin abinda ya haddasa mata ciwon nake son ku sani domin a ɗauki mataki….”
“Minene likita?”.
Daddy ya sake faɗa a zabure cikin katse Dr Khalifa Shira.
“Kwantar da hankalinka Alhaji”. Khalifa ya faɗa yana sake gyara zama. Cigaba yay da faɗin, “Ina son ku fahimci maganata da idon basira duk da ban sani ba ko kun san halin da take ciki kafin yau ɗin. Bincikemu ya nuna mana ba komai ya haddasa mata matsalar da take ciki ba yanzu sai Shaye-shaye..”
“What?!!”.
Daddy ya faɗa yana miƙewa zumbur. Jikinsa har rawa yake wajen nuna Dr Khalil Shira. “Yarinyar tawa zakaima sharri, miya haɗa wata Muwaddat da shaye-shaye? Yarinyar da bata san komai ba sai karatunta. Amma kai dai wlhy anyi…….”
“Yaya Please ka bari ya faɗa mana abinda ke faruwa mana. A wannan zamanin har wani gardama ko shaidar yaranmu za’ai akan hakan”. Uncle Yousuf ya faɗa cikin damuwa da takaicin Daddy. Mommy ma kallonsa take cikin tashin hankali da ɓacin rai, duk da ba itace ta haifi Muwaddat da cikinta ba bazata so ace yarinyar ta lalace kamar haka ba. Tasha wahala a hannun mijinta akan mahaifiyar Muwaddat matuƙa, bayan rasuwarta kuma tabar baya da ƙura dan Daddy wani sabon shafin wulaƙanci ya buɗe akan al’amarin Muwaddat gareta….
Bayanin da likita ya fara ne ya katse mata tunaninta. Dr Khalifa Shira ya cigaba da faɗin, “Alhaji a wannan zamanin da muke ciki wannan ba abin mamaki bane. Yara mata da yawa sun shiga wannan mummunar aƙidar abin tashin hankali harda matan aure ma. Iya gaskiyata na faɗa muku Muwaddat na shaye-shaye, kuma da alama ta jima a cikin wannan al’amarin dan gashi har ya fara taɓa mata lafiyarta. Idan kuma har bata dainaba komai zai iya faruwa ciki harda rasata. Ya dace kusa ido akanta da duk wani motsinta na rayuwa, idan da dama ma a nisantata da komai cikin hikima, sannan a rabata da duk abokan mu’amalarta akan hakan harma da inda take zuwa ta shawo dan alamu sun nunamin baku san tanayi ba. Iyaye da yawa sunfi maida hankali da damuwa akan kar ƴaƴansu mata su lalace wajen zubar da mutuncinsu akan huɗubar maza (zina), a tunaninsu wannan itace kawai matsalar dake iya tauye mace ko fanɗarar da tarbiyyarta. Shiyyasa sai yaran har suyi nisa a lalacewar da basu jawoma kansu tunaninta ba misali irin wannan ta shaye-shaye daketa ƙara yawaita a cikin al’ummar mu a yau. Hakama mazaje da yawa sakacinsu da son zuciya ya haifarma matansu da yawa shiga irin wannan halin batare da sun fargaba. Yayinda wasu ɓangare na matan kan jefa kansu ne ga ɗabi’ar shaye-shayen saboda son zuciya ko zama da abokai ko ƙawaye ko samari dakan koya musu. Ya kamata ku binciki silar faɗawarta wannan yanayin kuyi kuma gaggawar maganceta duk da abin ya rigada ya mata nisa sosai sai addu’a gaskiya. ALLAH ya bata lafiya ya kuma shiryar damu da zuri’armu baki ɗaya akan tafarki na gaskiya”.
Uncle Yousuf da Mommy ne suka iya amsawa da Amin. Daddy kam da alama ma hankalinsa sam baya jikinsa. Dr Khalifa Shira ya ɗan ƙara musu da shawarwarin yanda zasu fuskanci rayuwar Muwaddat ɗin. Kafin ya sallamesu. Har lokacin Daddy bai iya sake furta komai ba. Dan da zasu tafi ma sai da Uncle Yousuf ya taɓashi, sai dai yana yunƙurawa zai tashi juwa ta kwasheshi ya tafi zai zube ƙasa sai da suka taro shi. Hankali tashe shima aka bashi gado. Nanfa Jiƙamshi family suka sake shiga maɗaukakin tashin hankali mara misali.
Haka suka yini ranar zubir a asibitin. Shi kansa bai samu kansa ba sai wajen goma na dare bayan ya maida Aunty Saliha matar Uncle Yousuf gida da yaransa yace ya dawo masa da motar ya wuce kawai shi dole zai kwana anan saboda Daddy shima dole an bashi gado. Dr Khalifa kuma yace bazasu sallamesa ba har sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu da rai. Godiya yay masa da hakan dan harga ALLAH ya matuƙar gajiya dama ga yunwa dake cin hanjinsa kasancewar bai wani samu abincin kirki yaci a yinin ba sai wata ƴar gurasa. Sai dai babu yanda zai yi tunda hanyar neman abincinsa ce. Koda ya shiga gidan bai nema kowa ba ya shige ɗakinsa. Sai da ya kammala komai na al’adar rayuwarsa sannan yay zaman cin indomie ɗin daya saya wajen Haladu mai shayi. Tare da shayinsa daya sabarma kansa sha yaci, dan ya samu an dafa masa sabo a flaks. Yasan aikin ƙannensa ne dan basa gajiya da hidimarsa. Hatta ɗakinsa ƙal yake da gyara, dan ko kayansa ƙananu basa ƙyashin zama su wanke masa fes su goge, manyan kayanne dai irinsu shadda sai dai ya kai wanki. Badan kuma bazasu iyaba yake kaiwar, sai dan rage musu aiki ne. Ya jima baiyi barcin ba yana ƙullawa da kwancewa akan al’amuran rayuwa da suka haye masa badan ya tsara su a cikin rayuwarsa ba. Tun yana yaro a kullum burinsa shine buga ƙwallon ƙafa da yin kasuwanci, sai gashi yau ya tsinta kansa a wani matsayin ɓoyayyen aiki da ya zame masa haye. Dan lamarin wannan ɗan taran da bai san miye manufarsa ba yana sake kutso rayuwarsa cikin rayuwar mutanen da har yanzu ya kasa samun amsa ko dalilin dangantakar da ALLAH ya ƙulla a tsakaninsa da su batare da su sun san ma’anar hakan ba suma na cimasa rai. Su dai kawai kallon driver a ƙarƙashinsu suke masa kamar yanda Uncle Yousuf ɗin ya ɗakkosa tun farko yi. Sai kusan ɗaya da wani abu ya samu barcin ya ɗauke sa mai cike da mafarkai marasa daɗi da suka shafi Jiƙamshi family, kodan ya kwanta da tunanunsu ne a rai oho. Ai ko sai gashi ya kusa makara da asuba. Da ƙyar ya iya tashi yay alwala ya wuce massalaci…
Sashen Abba ya fara shiga kamar yanda ya saba a kowace safiya duk da sunga juna a massalaci. Gaishesa yayi cikin girmamawa da ƙanƙan da kai tare da masa bayanin komawarsa aiki jiya. Karan farko Abba yay ɗan murmushi irin na manya. Tare da faɗin, “Naji daɗin haka sosai, ina kuma maka addu’ar fatan alkairin ALLAH ya baka ikon jurewa. Aliy ba sonka bane banayi da kaga ina maka faɗa. Zaman nan naka ne bana so a hakan. Kai ba aiki ba, ba aure ba, ba wani sana’a ƙwaƙwƙwara ba. Ka duba ƙannen bayanka kusan huɗu sunyi aure har ma ana batun yima wasu ukun. Ba maganar mata nake ba dan su dama dan hakan ta faru ba komai bane ba ai tunda matane”.
“Kayi haƙuri Abba in sha ALLAHU zaku cigaba da samuna a yanda kuke fata. Ku gafarceni da duk ɓata muku da nake yi”.
“ALLAH ya yafe mana baki ɗaya, amma ka dage dai ka nema matar aure zamanka ya isheni haka, kaima ina son ganin jininka kafin ƙasa ta rufe idanuna”.
Ɗan murmushi kawai yayi kansa a ƙasa. Yau ya ɗan jima a wajen Abban har wasu a cikin ƙanensa suka ɗan shigo gaida Abban. Bayan barinsa nan cikin gida ya shiga. Kowane ɗaki sai da ya leƙa suka gaisa, a ɗakin Ammah ya ɗan sha shayi a tsaitsaye yay mata sallama ya fito ganin yana neman makara. Wanka yayi a gurguje yay shirinsa cikin uniform ɗin aikinsa ya fice a gidan….
★ Yau ma dai gidan Uncle Yousuf ya nufa kai tsaye, saɓanin jiya ya sameshi a compound zaune tare da baƙo. Bai zauna wajen maigadi ba ya nufesu. Uncle Yousuf dake dubansa da murmushi ya ce, “Uncle Smart na yara”. Murmushi yayi da ɗan shafa kansa suka gaisa cikin girmamawa. Baƙon nasa ma suka gaisa. Yana ƙoƙarin barin wajen Uncle Yousuf ya tsaida shi tare da nuna masa wajen zama. “Kaga zauna muyi magana shima ɗan gida ne. Dama kuma akan abinda ya shafi aikinka muke maganar. Sunansa Tajuddeen, surukina ne kuma ɗan uwana. Yaso Muwaddat da muka kai asibiti jiya kuma yana akan sonta dan har ranar aure an saka musu shekaru uku da suka gabata, sai dai taƙi yarda ai bikin. Abinda yasa nace maka zaman ya shafeka saboda taimakon da muke son kai mana ne tare da sake roƙonka kan ajiye aiki da kai niyyar yi. Aliyu a haɗuwarku ɗaya da Muwaddat kawai na fahimci zaka iya bamu taimako akanta, dan kafin kai mun saka drivers da yawa tun dawowarta ƙasar nan amma tsoronta sukeji saboda azababbiyar yarinya ce da kake ganinta, gashi bata shakkar kowa. Shiyyasa basa iya yin komai kan al’amarin ta. Akan Muwaddat kam nasan aikine mai wahalar gaske zamu baka amma dan ALLAH ka taimakemu kaine kawai hope ɗinmu a yanzu game da yanayin da take ciki.”
Ganin yanda yakai ƙarshen maganar kamar a yanayin son jin ta bakinsa ya sashi nisawa. Cikin dakewar nan tasa ya ce, “Alhaji zan iya taimaka muku, sai dai fa akwai matsala dan zamanmu inuwa ɗaya da ita bazai yiyu ba. Kayi hakuri bazan iya ɗaukar ƙasƙanci ba, idan tace zata wulaƙantani bana zaton kallonta matsayin wadda nakema aiki zan ɗauki mataki kanta ako ina ne kuma”.
“Na baka wannan damar, dan hakan nafi buƙata nima”.
“Shikenan, wane irin taimako kuke buƙata da ga gareni?”.
“Sanya mana ido akan al’amuranta, ƙawayenta, abokan mu’amalarta, inda take zuwa bayan wajen aiki. Kai hatta waya da zatayi idan san samune musan dawa take yi. Bayan ka gama sanin waɗan nan sai muje mataki na gaba”.
“Indai wannan ne babu damuwa in sha ALLAHU”.
Godiya sukai masa, tare da tabbatar masa zai fara aiki da ita da zarar an sallamota asibiti. Sun kuma ninka masa albashinsa……….✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣2️⃣
……..A ranar dai bai yi aikin komai ba sai zama tare da maigadi suka sha hirarsu, abinci ma daga cikin gidan aka kawo harda nashi. Yaso ƙin ci dan shi irin mutanen nan ne masu tsantsenin tsiya. Abu indai ba nasu ba kona gidansu sukan iya hana kansu koda suna buƙatarsa. A hakan ma kaɗan yaci ya cire hannu. Sai bayan sallar la’asar ya tafi kai Aunty Saliha asibiti tare da su Deen. Kasancewar da kayan abinci ta tafi ya taimaka mata wajen shiga da su ciki. Anan ne ya samu damar ganinta. Kwance take rai-rai a kan gado Mommy na zaune ta jingina da jikinta, a kallo ɗaya zaka tabbatar da taji jiki, dan kwana ɗaya kacal harta faɗa da ƙarayin wani fayau da ita. Bayan ya gaisa da su Mommy ya gaisheta da jiki itama a taƙaice. Kaɗan ta ɗago idanunta dake nuna yanayin halin da take ciki na ciwo ta dubesa. Maimakon amsa masa sai ta watsa masa wani kallon rashin mutunci ta ɗauke kai a yatsine.
Mommy ce ta dubeta cikin ɗan faɗa-faɗa. Sai dai kafin tai magana Deen ya ce, “Aunty Lu Uncle Smart fa na gaisheki da jiki baki amsa masa ba kuma kina masa harara”. Harara ta zubama yaron, muryarta a ɗashe irin na mai ciwo tace, “To maganatu naƙi na amsa ɗin, an kuma hararesan. Yaro sai sa idon tsiya. Ko dokace kowane trash idan ya gaisheni sai na amsa”. Baki ya tura mata da matsawa jikin uwarsa yana ɗan ƙunƙuni. Zata sake magana Mommy ta tareta. “Wai nikam yaushe ne zakiyi hankali Muwaddat? Yanzu kina a gadon asibitin ma bazaki bar masifa ba. Jiya i yanzu fa kina nan keba matatta ba keba mai rai ba hankalin kowa a tashe. Haba ayi mutum babu haƙuri sam sai baƙin tujaran tsiya kamar mara mafaɗi”.
Sosai ranta ya sosu ganin yanda Mommy ke mata faɗa a gabansa. Badai ta tanka ba amma tayi alƙawarin koya masa hankali tunda har akai mata haka a kansa. Bata sake magana ba ta gyara kwanciyarta ta juya musu baya, dan koyaya tana shakkar Mommy ɗin kasancewar bata yarda ta bata fuskar rainata ba duk da abinda Daddy kemata akanta tun tana a showal. Shima ficewa yay daga waje abinsa yana sake jinjina halin yarinyar mai ido a tsakar kai…
*_BAYAN KWANA UKU_*
Kwanakinta uku a asibitin aka sallamosu, dama shi Daddy tun washe gari aka sallamesa sai dai Dr Khalipa ya bashi shawarar ɗan yin nisa da asibitin har ya samu nutsuwa. Shiyyasa bai sake zuwa ba akan tsayawar Uncle Yousuf amma duk da haka kullum sai yazo da dare ya dubata. Alhmdllh jikin nata da sauƙi sosai. Sai dai har sannan batajin ƙarfinsa. Ga buƙatar kayan shaye-shayenta da take matuƙar yi sai dai babu damar shansu. Shine ya ɗakkota tare da Mommy. Yanda kowa ke tattalinta na bashi mamaki kamar wata ƙaramar yarinya. Musamman ma Daddy dake yi kamar zai maidata cikinsa. Ko yaya ta motsa sai ya tambayi ba’asi. Idan ko tace wash yaringa jera mata sannu kenan kaji har muryarsa na zuga dan damuwa. Kasancewar sallamar dare akai musu yana ajiyesu ya wuce gida. Da ƙyar ya samu napep saboda yanayin anguwar tasu. Ana sallar isha’i ya shiga gida. Wanka ya farayi sannan ya shiga gaida su Ammah. Yau kam ya samu Umma da Mama na rikici akan yara, duk da abune da bai cika faruwa ba a gidan irin haka kaga suna faɗa a zahiri sai da yaji ransa ya sosu. Aunty Amarya ce tamai bayanin tushen faɗan wai Mubarak ne ya daki Sakina saboda ya aiketa taƙi zuwa har ya jimata ciwo a gefen ido fuskarta ta kumbura. Ita kuma Mama tai magana akan ita bata hanashi dukansu idan sun masa ba dai-dai ba. Amma yasan inda zai daka saboda gudun nakasa mutum. Umma kuma dake kamar a jirace ta amshe faɗan shine fa suka rikice haka. Daga inda yake ya ƙwalama Sakinar kira, fitowa tai da ga ɗakinsu da taimakon Yayarta Khadijah. Hankalinsa ya tashi shima da ganin yanda kusan rabin fuskar yarinyar ya kumbura, gashi ciwon kamar ma akan idon ne ba gefe ba.
“Kawo mata Hijjab” kawai yace yana kallon Khadijan. Da to ta amsa masa. Su Umma dai nata sa’insar su Ammah na basu haƙuri. Shikam wayarsa ya cigaba da dannawa kamar ma bai san mi ake a gidan ba har Khadijah ta dawo. Mayafi ta kawo mata dan hijjab ɗin zai takura mata, baice komai ba yay gaba Sakina ta bisa a baya. A rukunin ɗakunsu na samari ya tsaya, kira ya dannama Mubarak dake ɗaki zaune shiru alamar akwai damuwar abinda ya aikata tattare da shi shima, dan tunda abin ya faru baya cikin nutsuwarsa yayi dana sani babu adadi, jin hayaniyar su Umma ta sake ɗaga masa hankali shine ya koma ɗaki ya rakuɓe.
“Fito nan ina son ganin ka”.
Bai gama ajiye wayar ba Mubarak ya fito dan suna shakkarsa sosai a gidan. Gaba yay suka bisa baya su duka biyun, kasancewar akan titi layin gidansu yake a ƙofar gida suka samu napep, shi da Sakina suka shiga baya, Mubarak kuma kusa da driver. Wani babban canix na anguwar tasu dake can ƙasa sukaje, yanda suka tarbesa da alama sun sanshi sosai. Dan babu ɓata lokaci aka hau duba Sakinar. Bayan an rufe ciwon da bandeg mai camix ɗin ya basu shawarar kaita asibiti da safe gudun kar idonta ya taɓu. Godiya ya musu ya biya kuɗin suka fito. Dama Uncle Yousuf ne ya bashi su da safe dubu biyar.
Sun sami gidan yanzu tsit, dan Umma da Mama na gaban Abba da ya gama musu tijara yace kuma su sameshi. Suna shigowa Sadiq yace suje Abba na kira. Su kaɗai suka shiga shi kuma yay shigewarsa ciki, ya zauna sun fara gaisawa da Amma Sadiq ya shigo shima yace yazo Abba na kiransa. Miƙewa yay yabi bayansa. Ya samu Abban nata zagin Mubarak, shi kuma kansa a ƙasa kamar ma yana kuka. Koda ya zauna yana kallon yanda Umma ke hararsa. Bai damu ba ya fuskanci Abban dake cigaba da zagin Mubarak.
“Abba ayi haƙuri haka nan, yayi kuskure kuma dama nima zan hukuntashi akan laifinsa duk dai ya amsa laifinsa kuma ya bada haƙuri da yin nadama. Itama kuma tace ta yafe masa, amma duk da haka so nake taji sauƙi sai na zauna da su…”
“Ikon ALLAH ƙarfin hali, ni kana bani mamaki a gidan nan Hydar. Ka dinga wani ɗaukar gabara kamar kaine ubansu. To ko Salim dake yayanku gaba ɗaya yana wannan aikin ne? Ko sai kai sarkin iya zartar da hukunci…”
Tsawa Abba ya daka mata har sai da ta zabura. “Ke Usaiba ki kiyayeni a gidan nan. Da kike faɗin kamar ubansu ai uban nasu ne shi tunda babba yake garesu. Shi Salim ɗin dake babba miya amfanama kansa ma balle wani, shiko da kike ganin bai miki dai-dai ɗin ba tsaye yake akan tarbiyyar har ƴaƴanki. Badan Aliyn ba a gidan nan sai ƴaƴan ɗakinki sunfi kowa zamemun fanɗararru saboda banzan halinki nason ƴaƴan tsiya. Wlhy sonai ma ya masa dukan mutuwa shima ya fasa masa ido kamar yanda ya fasa mata…”
“Saboda ita ƴar sonka ce da uwarsa. To wlhy ya dakesa ai gashi nan yaga in ban rama masa ba. Har yau ne yabo ya tashi a kansa gareka. Da kake kiran Salim mara amfani wlhy sai dai in shine mara amfanin. Dan koba komai yarona nada iyalinsa da gida da motar hawa ga aiki bashi dake yawon gal-gal ba babu makama sai watsewa a gari. Auren ma da zai ajiye iyali ya gagara sai bin ƴaƴan mutane ana lalubewa a sorayen iyayensu, da yake tsoron uwarsa kakeji ka kasa magana…”
Sosai ya rumtse idanunsa dan jin zafin maganganun Ummar garesa. Cikin dakewar nan tasa da sanyaya harshe ya ce, “Dan ALLAH Abba kuyi haƙuri abar maganar. In dai Mubarak da Sakina ne zan hukuntasu akan laifinsu.”
Mama da tun ɗazun batace komai bace ta karɓe zancen da faɗin, “ALLAH yay maka albarka ɗan halak, wannan shine girma na gaskiya ga babba Hydar, ba ɗagawa da alfahari akan abinda ALLAH shine mai badawa ba. Koda yake iyakar mutum ma alfaharin kawai tunda bai isa tanƙwara ɗan ya masa yanda yake so ba sai dai yaga yanama iyalansa”.
A take falon ya nema sake rikicewa tsakanin Umma da Mama ɗan kai tsaye dai akan Salim ɗin da Umman ta gama kurantawa ne Mama ta yaɓa mata magana. Wata gigitacciyar tsawa Abba yay musu data sakasu nutsuwar dole su duka. Dan dama shi kam a yanzu ne kura tai lafiya saboda girman shekaru da yau da kullum. Amma tsayayyen mutum ne a gidansa kusan ma halayensa ne Uncle Smart ɗin ya ɗakko a gidan. Masifa sosai ya musu tare da wankesu tas. Shi dai bai sake magana ba har Abban ya gama ya sallamesu. Koda suka shigo gidan Umma nata cigaba da ƙananun maganarta kamarma zata maida faɗan kan Amma ne. Ammah nunawa ma tai bata san da ita take ba. Duk da ita mutum ce mai zafi da rashin ɗaukar raini, mace ce mai kawaici musamman akan al’amurin yaranta. Dole Ummar dai tagaji tai shiru dan kanta. Koda Uncle Smart kuma ya koma wajenta bai mata maganar abinda ya farun ba, ba kuma ta tambayesa ba, ya ɗan tsakuri abinci ya ƙarama su Asma’u karatun Alkur’ani da suke jiransa.
Koda ya koma ɗaki ya jima maganganun Umma na masa kai kawo a zuciya da ruhi, yana jin matuƙar ciwo da zafi a duk sanda aka zagesa da ƙaddararsa a gidan musamman akan aiki. Dan shi akan aure bawani yana gabansa bane har yanzu. Zaima iya rantsewa bayan Kubrah ɗiyar ƙanwar Ammah da suka haɗasu daga ƙarshe iyayenta suka wargaza abun wai akan baida aikinyi bai taɓa tsayawa da ƴar wani da sunan soyayya ba. Ko ita ɗin da farko ko kallo bata ishesa ba, sai da Ammah ta zaunar da shi ta masa nasiha kasancewar gwaggon tasu ce ta buƙaci haka da kanta saboda son da yarinyar ke masifar masa. Har ranar aure an saka musu kafin abubuwa su rikice iyayen suga mai kuɗi suka canja shawara. Ko a yanzu haka da yarinyar ke’a gidan aure tana masifar son sa, dan a duk sanda ALLAH zai haɗasu sai tayi kuka dan ma baya nuna ya fahimci mitake ciki ne……..✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣3️⃣
_______________________
……..Washe gari da ranakun da suka biyo baya babu wani ƙwaƙwƙwaran aiki da yayi kasancewar wadda aka ɗaukesa aikin a yanzu da ita bata fita. Sai dai yaje ya zauna wajen masu gadi har lokacin tashi yayi ya koma gida. Ganin hakan yasa yau bai fita da wuri ba yabi su Maryam makaranta kamar yanda yakan yi lakaci zuwa lokaci batare da sun sani ba. Yakan ɗan binciki halin da suke ciki da yanayin karatunsu. Sai goma yabar makarantar. Lokacin da ya iso gidan aikin nasa sha ɗaya saura kaɗan. Tunda ya turo gate ɗin ya shiga akanta ya fara sauke idanunsa. Tsaye take a can jikin wata farar mota da ke ƙaton compound ɗin nasu. Kallo ɗaya da yay mata bai sake marmarin ƙarawa ba saboda shegun kayan da ke jikinta. Skert ne blue da ya kamata ɗam-ɗam ya fidda mata halittar jikinta da ƙyau, sai ƴar riga mai santsi kalar gwaiduwar ƙwai. Babu ko ɗigon kwalliya a fuskarta sai wani ƙaton glasses data toshe idanunta da shi, kanta da hula irin ta zamani da ake yayi. Dan ƙyau kam tayi ƙyau, sai dai ga ɗabi’a da tarbiyyar ɗiyan musulmi bahaushen arewacin Najeriya babu abinda shigar tata ke nufi ga duk wanda zai kalleta sai ƙarancin tarbiyya da wayewar banza. Ga wayayyu kuma irinta hakan normal ne.
Tsaki ya ɗan ja a ƙasan maƙoshi yana ƙara tsuke fuska. Su maigadi dake zaune kamar a tsorace duk ya bama hannu suka gaisa. Yanda suke kamar a noƙe ya bashi mamaki. Sai dai yana niyyar kaiwa zaune mai wanki ke faɗin, “Ɗan uwa Hajiya Muwaddat fa kai take jira. Tsaiwar da kaga tayi can tun ɗazun take zuba tijara har mu ma nan sai da muka samu rabonmu na zagi, kasan ita sanda aka raba mutunci tana cikin bargo ƙudindine shiyyasa bata samu ba”.
Shiru kamar bazai amsa ba. Sai kuma zuwa can a dake ya ce, “Tunda kun maida kanku sakarkaru gareta ba”. Da ga haka yaja bakinsa ya tsuke tare da ciro wayarsa da ga aljihu zai fara sana’ar danne-dannen nasa. Wata irin gigitacciyar tsawa Lulu data gama kaiwa wuya da takaicinsa ta daka masa. Sai dai ko gezau wai an tsikari kakkausa. Cikin takun nan nata na izza da yanga ta ƙaraso gate ɗin. Ashariya ta mulmulo tare da faɗin, “Wai kai ɗan uban wanene? Mi kake taƙama da shi ne, tsabar kai cikakken mara mutunci ne kazo a makare ina tsaye tun 8:30 ina jiranka amma kazo ka zauna anan irin ma kai baka gannin nan ba. Na rasa mi Daddy da Uncle Yousuf suka gani gareka suka takura da sai kai ne zaka zama driver na a gidan nan illiterate irinka..”
A hankali ya rumtse idanunsa sai kuma ya buɗesu a kanta. Wani irin yankawa zuciyarta ta shigayi da sauri-sauri, dan wani irin kwarjini mai cika idanu yay mata. Amma saboda tsabar ƙarfin halinta da taurin zuciya sai ta cigaba da masifar kamar zata cinyesa ɗanye. Harda cewa sai tayi maganin rawar kansa a gidan. Sosai su maigadi ke’a rikice. Shiko yanda ya dake sai ma ka ɗauka ba dashi takeyi ba. Dan tuni ya maida hankalinsa ga wayarsa…
“Wai ya akayi ne?”.
Mommy da hayaniyar Lulu ke zuwa mata cikin kunne sama-sama tun ɗazun ta fito dan ganema idonta ta faɗa tana ƙarasowa. Cikin masifar nan tata ta juya tana faɗama Mommyn abinda yay mata. Dai-dai nan shima Daddy ya fito da alama ma wanka ya fito dan bathrobe ce a jikinsa. Mommy ta juya ga Uncle Smart, sai dai kafin tace masa komai ya shiga gaidasu ita da Daddyn da sai yanzu Mommy da Mawaddat suka lura da shi cike da girmamawa kamar bashine ya watsar da al’amarin Lulu ba tun ɗazun. Cikin kulawa suka amsa masa, Daddy ya dubesa cikin alamar sanyin yanayin daya riskesa a kwanaki biyun nan akan halin da Lulu ke ciki tare da faɗin, “Ya akai ka makara haka Aliyu Hydar?”.
Bai iya ƙarya ba ko kwana-kwana. Sak yake shi akan komai. Dan haka kai tsaye ya ce, “Alhaji na ɗan biya ta school ɗin ƙannena ne dan sanin halin da suke ciki akan karatunsu tunda naga kwana biyu ba wani waje nake zuwa ba”.
Lulu zatai magana a hargitse Daddy ya katseta cikin lallashi. “To kiyi haƙuri haka tunda dai kinji uzirinsa ai ko Babyna. Kuje ya kaiki haka nan rana na ƙarayi wannan gyaran jikin naki dake ɗaukar lokaci kamar za’a sauyaki”.
Takaici kamar ya kashe Mommy da ke kallon mijin nata. Sai dai batace komai ba.
Lulu dake wani cika da batsewa ta ce, “Amma Daddy kana ganin kofa haƙuri bai bani ba. Tsabar wulaƙanci kallo ma ban ishesa ba balle gaisuwa sai da Mommy ta fito ma ya taso da ga inda yake zaune tsabar shi mashahurin mara mutunci ne”.
“Oh oh”.
Daddy ya faɗa yana dafe kansa. Sai kuma ya dubesa da faɗin, “Kaga dan ALLAH bata haƙurin nan a rabu lafiya kaji Aliyu”.
A harzuƙe ta ce, “Bana buƙatar haƙurin nasa Dady, sai da aka roƙa min. Ka barsa zanyi maganinsa tare da sauke masa girman kansa, banza mutum ba kowan kowa ba sai ɗaukar kai wata tsiya kana driver. Shiyyasa na tsani irin jahilan nan da ko primary basu yi ba sai ji da kai motsoww!!”.
Maganganun ta sun masa zafi, amma sai ya miƙe kodan darajar Daddy da Mommy. Key ɗin jikinsa ya ciro yana nufar motar. Tsawa tai masa tare da wurga masa wani key ɗin. “Ba ita nake so ba stupid Men! illiterate kawai”.
Key ɗin data jefa masan yabi da kallo na kusan minti ɗaya, kafin ya ɗago ya ɗan kalleta sai kuma ya ɗauke kansa yana mai cije lips ɗin sa ya ɗauka batare da yace komai ba nan ma. Daddy ya ɗan girgiza kansa da faɗin “ALLAH ya shiryeki Muwaddatan-warahamah. Koda ya gyara motar zuwa gabanta ƙin shiga tayi. Daddy da ke tsaye zaman jiran ganin sun fita lafiya yay masa nunin ya fito ya buɗe mata. Bai musa ba ya fito fuskarsa na karayin wani kicin-kicin. Batare daya kalleta ba ya buɗe mata ƙofar. Sai da taja tsaki da faɗin, “Motsoww! baƙauye kawai da ko aikinsa bai sani ba” sannan ta shiga. Maidawa yay ya rufe suka fice a gidan. Karan farko Mommy ta saki murmushi, dan tabbas tasan a wannan haɗin akwai ƙura. Lulu masifa da izza. Aliyu jan girma da rashin ɗaukar raini. Taga dai yanda wasan zai cigaba da kasancewa tsakanin ɓera da mage.
Karaf murmushin Mommyn a idon Daddy da ya juya zai koma ciki. Ya wani ɗaure fuska da faɗin, “Aniyarki ta biki idan ma wani abu kike ƙullawa akan yarinyata”.
Sarai Mommy ta jisa amma sai bata tanka ba, dan ta fahimci masifa yake nema da ita akan Muwaddat ɗin tunda suka dawo asibiti. Itako taƙi bashi kowacce irin damar cimata mutunci dan a yanzu kam bazata ɗauki abinda ta ɗauka a baya ba kan Mahaifiyar Muwaddat ɗin da ita kanta yarinyar. Suna shiga ciki tai wucewarta ɗakinta bata bisa ba duk da ƙananun maganar daya cigaba da faɗa masu ƙona zuciya. Har da cewa ƙilama itace taima Muwaddat ɗinsa asiri take shaye-shaye saboda tana baƙin ciki da ita a gidan. Tana shiga ɗaki ta fashe da wani irin kuka mai cin zuciya. Sai da tai mai isarta ta share hawayenta, dan duk yaran sun wuce makaranta da ga ita sai masu aiki. Duk yanda take jurewa da dakewa akan al’amurin mijin nata game da ƴarsa a yanzu hakan yana neman fin ƙarfinta. Dan al’amarin akwai ciwo sosai matuƙa gaya. Cikin ƙanƙanin lokaci tai ninƙaya a tunanin shekaru ashirin da shida da suka shuɗe kafin yau….
*_SHEKARA ASHIRIN DA SHIDA DA SUKA SHUƊE_*
Malam Ibrahim Jiƙamshi shine sunan mahaifin su Isma’il (Daddy), yayinda Malam Salisu Ibrahim Jiƙamshi ya kasance ƙaninsa ɗaya tilo da iyayensu suka haifa (Mahaifinta). Sun rasa iyayensu tun suna ƙananun yara, dan haka suka tashi da tsananin ƙaunar juna da shaƙuwa a hannun kakarsu Iyan Jiƙamshi. Iyan Jiƙamshi kakarsu itace har taga aurensu su duka biyun, dan ALLAH yay mata rasuwa ne bayan haihuwar Isma’il da ita Kareema. Duk da bawani wayone da su sanda ta rasu ba bazasu iya manta wasu ƴan abubuwa da suka shafeta ba. Iyan Jiƙamshi ita tabarma Ibrahim da Salisu wasiyyar haɗasu aure idan sun girma, ba komai yasa haka ba sai ganin yanda Isma’il (Daddy) ke yawan kaffa-kaffa da ita tun tana jinjira kasancewar ta ita ɗaya ƙanwarsa da yake gani. Bayan rasuwar Iyan Jiƙamshi da shekara biyu ALLAH yayma mahaifinta Salisu rasuwa shima. Wannan mutuwa ta matuƙar girgiza Ibrahim matuƙa da har takaisa da baro garin Jiƙamshi gaba ɗaya ya dawo cikin Kano tare da ita Kareema daya amshe wajen mahaifiyarta dan bayan ta kammala takaba anta bashi shawaran aurenta ciki harda mahaifiyar su Isma’il (Daddy) amma yace bazai iya ba. Bazai taɓa iya auren matar ƙaninsa Salisu ba. Wannan daliline yasa iyayenta cewa ta bashi ƴarsu tazo gida ta samu miji. Ba rabuwar daɗi akayi ba, dan mahaifiyarta ta tafine ta barta tana kuka mai tsanani, haka ma Ibrahim da matarsa da Isma’il. Riƙonta ya koma hannun iyayen Isma’il (Daddy), inda suke tattalinta da kulawa matuƙa su da ɗan su Isma’il. Dawowarsu Kano da shekaru uku aka haifi Yousuf, inda ALLAH yayma mahaifiyarsu rasuwa itama a wajen haihuwarsa. Abubuwa sun sake rikicewa, inda mutuwar ta sake taɓa rayuwar Ibrahim matuƙa har sai da ta zama sanadin kamuwarsa da ciwon ajali shima. Yayi jinya sosai ta kusan shekara takwas, yayinda ita da Isma’il suka raini Yousuf tamkar uwa da uba a garesa……….✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣4️⃣
______________________
……..Wannan haɗin kan nasu da ƙaunar juna ya ɗan dinga ragema Malam Ibrahim raɗaɗin ciwo, dan duk da yana kwance a duk sanda suke tattalin Yousuf a tare kamar wasu mata da miji duk da ƙarancin shekarunsu sai yaji farin ciki har fuskarsa kan nuna hakan. Gashi shima suna kulawa da shi matuƙa sai kace wasu manya. Yana da shekara biyar kwance ya yanke shawarar ɗaura musu aure saboda halin rayuwa, a lokacin shekarar Isma’il goma sha tara a duniya. Itako nada goma sha huɗu. Maƙwafcinsu ne ya jagoranci komai, ranar wata juma’a sun dawo makaranta Isma’il ya gama jarabawar ƙarshe ta kammala sakandire, ita kuma jsce suka iske an ɗaura musu aure. Ita bata wani ɗauki abin da muhimmanci ba, kasancewar da sauran ƙuruciya a tare da ita. Sai ma biyema Yousuf dake da shekara biyar a duniya tai suna murnarsu. Yayinda Isma’il ya shiga yanayin damuwa, dan shi harga ALLAH kallon ƙanwa yake mata uwa ɗaya uba ɗaya bawai matar dazai iya aure ba. Lura da hakan da Malam Ibrahim yayi ne ya sashi zaunar da shi yay masa nasiha mai ratsa jiki data saka jikinsa yin sanyi, tun kuma da ga wannan lokacin ya fara koyama kansa sonta ita Kareema (Mommy) tunda dama akwai ƙauna ta jini da shaƙuwar zaman waje ɗaya a tsakaninmu. Karatu muka cigaba da yi abinmu batare da anyi maganar tarewa ba, haka shima Yousuf an sakashi makaranta, gefe kuma muna cigaba da jiyyar babanmu malam Ibrahim. Isma’il na shekara ta uku a jami’a, ni kuma shekarar ƙarshe a sakandire jikin Baba ya sake rikicewa, ganin haka yasa maƙwafcinmu da muka zama tamkar ƴan uwan jini a yanzu shirya bikinmu ni da Isma’il dan yana fatan gani kafin yabar duniya. Haka ɗin kuwa akayi, aka gyara gidan tare da kawo abubuwan da suka dace da amarya sati ɗaya da kammala jarabawata ta ƙarshe akasha biki. Anan dai gidan muka tare, inda kwanaki goma sha ɗaya da tarewar tamu ALLAH yayma Baba rasuwa shima. Mun shiga ruɗani da tashin hankali matuƙa irin wanda bazai misalu ba. Dan da ƙyar al’amura suka daidaita mana bayan wani lokaci. Mun cigaba da rayuwa cikin shaƙuwa da soyayya mai ban mamaki, ga ɗan ƙaninmu Yousuf da muke tattali matuƙa, inda wanda bai sani ba zai iya ɗaukama ɗan mu ne sai idan ka kalleni ne zaka san ban kai haihuwarsa ba. Alhamdullah Isma’il ya kammala jami’a bayan rasuwar Baba da shekara biyu, ya kuma samu result mai ƙyau. Haka shima Yousuf ya shiga fimare 4. Burina a kullum shine na koma makaranta na cigaba da karatu nima, sai dai Isma’il na lallaɓani akan na bari ya samu aiki abubuwa su sake warware masa. Banyi musu ba nayi haƙurin, cikin ikon ALLAH kuwa sai ga aiki ya samu cikin sauƙi kasancewar a wancan lokacin ma neman masu irin kwalinsa ake ido rufe suna yanga dan aiki saima sun zaɓa. Wannan samuwar aiki shine mafarin komai, dan daga lokacin abubuwa suka fara canja salo a saɓanin yanda nake kallonsu ko na tashi na sansu.
*_Alhaji Sufi Ado Garko_* shine ya kasance ogan Isma’il a wajen aiki, mutum ne mai tarin dukiya da mutunci. Bashi da mugunta da ƙeta, dan ba aikin gwamnati kawai ya dogara da shi ba ɗan kasuwane babba da akeji da shi sosai a lokacin. Ƙwazo da amanar Isma’il ta fara janyo masa soyayya a wajen Alhaji Sufi ya fara jansa a jikinsa tare da ɗorashi akan wasu harkokinsa na kasuwanci a bayan fagen aikinsu na gwamnati. Alhamdullah wannan al’amari ya fara canja mana rayuwa, dan kuɗi sun fara shigowa Isma’il fiye da farkon samun aikinsa. Inda ya cika alƙawarin maidani makaranta, shima Yousuf ya shiga Sakandire. Shekarata ɗaya da komawa makaranta sai ga ciki. Isma’il da Yousuf da ni ɗin kaina mun shiga matuƙar farin ciki da baida misali. Na haihu lafiya bayan ciki yakai haihuwa, inda ALLAH ya bani ɗa Namiji wanda yaci suna Ibrahim muna kiransa da Abba. Na cigaba da rainon Abba koma nace Yousuf ya cigaba da rainonsa, dan tattalin yaron yake tamkar ƙwai a cokali. Sai dai ALLAH baiyi mai zama bane yanada shekara ɗaya da wata uku ya rasu. Yousuf ya sha kuka sai mune muka koma lallashinsa. Sai dai me ashe a lokacin ma ina maƙale ne da ciki batare da mun sani ba. Sai bayan rasuwar Abba ne ya bayyana. Munyi murnar hakan na cigaba da rainon ciki da karatu, yayinda ALLAH keta ƙara ɗaukaka Isma’il ta silar Alhaji Sufi Garko. Bayan isar cikin jikina haihuwa shima na haifesa, sai dai wannan karon ƴan biyu ne duk maza. Wayyo murna zo kaga farin ciki a wajen Yousuf da Isma’il dama ni kaina. Yara sun sake cin sunan Ibrahim da Salisu iyayenmu. Ana kiransu da Hassan da Hussaini ɗinsu. Bayan haihuwar ƴan biyu da shekara biyu na kammala karatuna, sai dai Isma’il yace bazanyi aiki ba sai da naita roƙonsa ni da Yousuf harda kukanmu sannan ya amince. Shine ya amshi takarduna da kansa domin nemamin aiki kamar yanda ya sanar min mai-gidansa Alhaji Sufi Garko yace ya kawo zai sama min gurbin a kamfaninsa insha ALLAHU. Kasancewar yace ya kai masa takardun gida a cikin weekend ya sakashi shiryawa ranar wata asabar. Wannan shine karo na farko a rayuwarsa da zai je gidan ogan nasa. Tare da Yousuf suka tafi, inda akai musu tarba ta mutuntawa, gidane katafaren gaske da ya basu mamaki, dan a ranar suka sake tabbatar da lallai Alhaji Sufi Garko mai kuɗi ne sosai. Suna zaune a falon Alhaji Sufi da aka saukesu saboda karamci saɓanin falon baƙi ƴarsa ƙyaƙyƙyawar budurwa data dawo daga karatu da ga ƙasar larabawa ta shigo falon amsar saƙo wajen mahaifinta. Tunda ta ɗora ido akan Isma’il ta kasa ɗaukewa, dan Isma’il ƙyaƙyƙyawan mutum ne ɗan gaye sosai, ina faɗa muku zancen gaskiya ne badan yana mijina ba. Ba Isma’il kawai ba hatta Alhaji Sufi ya lura da irin kallon da ƴar tasa kema yaronsa na ƙurilla. Yayinda Yousuf shi kuma abin ya bashi haushi saboda kishina ni ƴar uwarsa. Wasa-wasa Muwaddat ta kasa barin falon tana manne da su har suka bar gidan duk da bayan gaisuwar shi Isma’il bai sake kulata ba ma. Aiki dai an ɗaukeni ta silar Alhaji Sufi, sai dai tunda Yousuf ya bani labarin ƴarsa da abinda ya faru naji komai ya fitamin arai. Ban dai yima Isma’il maganar ba, amma kullum cikin kasa kunne nake naji abinda zai biyo baya. Shiru-shiru banji komai ba har na shiga wata shida da fara aiki ga kuma ciki ya sake samuwa. Abinda ya bani mamaki a wannan karon Isma’il bai wani nuna murnarsa sosai akan cikin ba kamar nasu ƴan biyu da Abba. Sai dai banyi magana ba. Bayan haka al’amuransa da yawa sun ɗan fara canjawa a yanda na sansu. Zai fita aiki da sassafe batare daya karyaba yanzu, bai dawowa kuma sai goma na dare. Wani lokacin ya tsakuri abinci, wataran ma baya ci sai yace min ya ƙoshi a gajiye yake. Tun bana ɗaukar al’amarin wani abu har ya fara damuna naima Yousuf maganar. Shima da yake yaro ne mai hankali da lura ashe ya fahimta yay shirune kawai. Kuɗi na sake shigoma Isma’il abubuwa na ƙara rikicewa a tsakaninmu da ban san kansu ba, dan haka Yousuf dake ƙoƙarin kammala sakandire ya lallasheni akan zai bincika. Yaron nan shine yay ƙoƙarin binciko mana komai, inda ya gano ashe Isma’il soyayya suke da Muwaddat ta bugawa a jarida, saboda shi ma yanzu haka ta koma aiki ma’aikatarsu. Hankalina ya tashi da gani har Yousuf, inda duk yanda naso danne abun a raina na kasa Isma’il na dawowa na taresa da maganar. Da farko naga shock a fuskarsa, amma da yake halin maza sai ya dake ya shiga borin kunya akan wane munafuki ne yay masa sharrin nan. Ƙin faɗa masa nayi, amma duk da haka yace yasan Yousuf ne. A daren ya tado Yousuf da ga ɗakinsa ya zagesa tas. Hakan da yay ya sake ɓata min rai muka kwasa da shi sosai abinda bai taɓa faruwa ba har ya kaisa ga marina, ya kuma tabbatar min nama shirya aure shi da Muwaddat babu fashi sai dai mu mutu ni da Yousuf ɗin. Kamar yanda ya faɗa kuwa ya cika, dan baifi sati biyu dayin rigimar tamu ba aka tsaida bikinsu shi da Muwaddat. Wannan tashin hankalin dana sakama kaina saboda yanda ya sake birkicemana a gidan ni da yaran da Yousuf yasa cikin jikina ya ɓare. Bai nuna ya damu ba ya cigaba da shirye-shirye aurensa. Inda Alhaji Sufi Garko ya ce ƴarsa fa tace bazata zauna a gidan da muke ba. Dan haka ya bashi mukullin ƙaton gida da dalleliyar motar hawa, nima mota da kayan faɗar kishiya kai kace ma nice amaryar kuma wai da ga gidan iyayenta. Shima Yousuf da ƴan biyu da nasu hidimar. Wannan abu ya sake ɗagamun hankali dan a ganina Isma’il dai auren jari ma yake shirin yi. Taruwa mukai muka tada masa hankali ni da Yousuf amma yace ko zamu mutu auren Muwaddat babu fashi wlhy. Hakan kuwa akayi, dan wata ɗaya kacal da komawarmu sabon gidan da ya zama dole garemu akai bikinsa shi da Muwaddat……..✍️
*_Karku rikice wannan Mawaddat ɗin mahaifiyar Lulu ƙamshi ce ba Lulun muke nufi ba😂_*
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣5️⃣
________________
……..Anyi shagalin biki kam na nunama tsara, dan har a gidan tv na ƙasa da jiha an nuna. Kuɗi sunyi kuka abin sai wanda ya gani. Mudai namu ido ni da Yousuf dan ko shagali ɗaya bamu halarta ba Isma’il ya hanamu wai baƙin ciki muke masa. Amarya ta tare ita da abubuwan ban mamakinta. Dan kuwa dai Mawaddat ta shigo gidan ne a tsaitsaye da tarin gadararta irin na ɗiyan wasu masu arziƙin. Dan sai da takai hatta kwanakin girkina wani lokacin Mawaddat cemin take wai ta saya tazo ta diremin kuɗi a gaban Isma’il baya cewa komai kuma. Akwai lokacin da sai da nai wata guda babu miji, dan kuɗi maƙudai tazo ta diremin wai ta sayi kwanakin girkina na wata ɗaya dan tana buƙatar hutawa da mijinta yanda ya kamata. Nayi kuka nayi kuka har na rasa hawayen zubarwa a wannan lokaci, sai Yousuf ne ke lallashina shima idan ya koma gefe yasha kukansa dan yanzu tsakaninsa da ɗan uwansa da ga faɗa sai ƙyara. Wannan damuwar tasa yana kammala sakandare da Mawaddat tace ta samar masa gurbin karatu a ƙasar ƙetare bai wani ja zancen ba ya amince ya tafi dan gara ya bar musu gidan. Tafiyar Yousuf ta sake sakani a cikin ƙuncin rayuwa dan abubuwa sun sake rikicewa sosai tsakanina da Isma’il. Takai yanzu sai dai su shirya su tafi yawon shakatawarsu ƙasashe daban-daban su huta sannan su dawo. Ɗan fita aikin da nakeyi ne yake ɗan ragemun nauyin zuciya, amma sai rana tsaka Isma’il ya hanani fita aiki wai ya dakatar dani. Ban taɓa shiga damuwa ba irin wannan lokacin, dan takai ko kuka ma na daina iya yi sai na zuci kawai. Dole kuma nabar aikin na cigaba da fuskantar matsalolin gidan masu ƙona zuciya. Ashe wasa farin girki, dan kuwa ba’ai komai ba sai da ciki ya bayyana a jikin Mawaddat, naga abu iri-iri wasu ma bazasu faɗu ba. A haka na cigaba da haƙuri sai dai na rungumi ɗiyana nai kuka na share hawaye har ALLAH ya kai wannan ciki watan haihuwa lafiya suka fara shirin tafiya ƙasar waje wai haihuwa. Sai dai kuma suna nasu ne ALLAH yana nashi, dan suna saura kwana biyu su wuce Mawaddat ta tashi da naƙuda, ga shi lokacin Isma’il ya fita gidan. Naso shareta dan ihun kuka sosai ta dingayi har part ɗina ina jinta, sai dai kuma na kasa saboda hakkin maƙwaftaka da daraja irin ta ɗan adam. Karan farko dana shiga sashenta, haɗuwa kam ya haɗu iya haɗuwa, dan ma ban iya masa kallon tsaf ba saboda halin da take ciki. Ni ɗin dai maƙiyyarta ni na taimaketa, ganin yanda take murƙususun kuka da ihun naƙuda gashi inata kiran Isma’il yaƙi ya ɗagamin ya sani samo ruwa nai mata addu’a a ciki, ina ƙoƙarin bata dai-dai nan ya shigo gidan, da wata irin sassarfa yay kammu, babu wani tunani ko bin ba’asi yasa hannu ya kaɓe ruwan, sai dai harta rigada tasha. Sosai ya balbaleni da masifa yana tabbatar min da duk abinda ya samu matarsa bazai barni ba. Kuka na fashe da shi ina masa bayani amma bai sauraren ba ya ɗauketa sukai asibiti tana kukan faɗin na yafe mata dan ALLAH. Tausayi ta bani, dan haka na bisu har harabar gidan ina faɗin, “Na yafe miki Mawaddat, ALLAH ya saukeki lafiya, nima ki yafemin”. Da ƙyar ta iya furta “baki mun komaiba sai alheri” dai-dai yana sakata a motar. Dazai barni dana bisu, amma rashin ganin fuska da ga garesa ya sani haƙura na bisu da addu’a zuciyata duk babu daɗi, ga jikina yay matuƙar sanyi da ganin yanayin nata.
Kafin su isa asibiti ta haihu a mota dan haihuwar tarigada tazo, gaba ɗaya ya rikice yama rasa miya kamata yayi, ga holdup da suka samu a hanya da ƙyar suka fita, kafin su isa asibiti Mawaddat ta zubda jini sosai har jikinta ya saki. Ko taɓata likitocin basu kai dayi ba UBANGIJI ya amshi abarsa, sai jaririya da aka samu gyarawa. Bayyana muku irin tashin hankalin da Isma’il ya shiga da wanda na fuskanta a garesa ma ɓata lokaci ne. Dan duk da bayanin da likitoci sukai masa akan dalilin rasa ranta cayay sam bai yardaba nice na kasheta, dan ya samu ina bata abu. Wasa-wasa rigima tai girman da har sai da hukuma suka shiga ciki, ALLAH ya soni mahaifinta mutum ne da yasan abinda ya kamata, shine ya balbale Isma’il ɗin da masifa tare da bani kariya har ALLAH yasa zancen ya mutu. Sai dai fa Isma’il ya koma mana kamar wani zautacce, jaririya kuwa tana manne da shi ya hana kowa ɗaukarta har iyayen Mawaddat. Duk kuma yanda sukai masa kurari da jan ido bai basu ɗin ba dole suka barshi da kayarsa. Randa akai addu’ar bakwai mahaifin Mawaddat Alhaji Sufi Garko ya raɗama yarinya sunan mahaifiyarta Mawaddat. A taƙaice dai Isma’il shine ya koma rainon Mawaddat da hanunsa, yayinda soyayyar mahaifiyarta kacokan ta koma kanta, tare da tausayinta. Komai shine kema yarinyar, a saboda ita ya ajiye aikinsa ya koma rainonta. Ko motsi idan tana barci babu wanda ya isa yayi. Idan kuma akayi kosu ƴan biyu ne ya kamasu yay musu dukan mutuwa. Nasha shan mari a wajensa saboda Mawaddat. A haka yarinyar ta taso a taɓare babu kwaɓa komai sai wanda take so za’ayi. Lokacin data isa shiga makaranta ya sakata a mafi tsada dake cikin garin na Kano, Islamiyya ce dai dole ya barta atasu ƴan biyu saboda tsayawar Yousuf da ya kammala karatunsa ya dawo, sai dai bai yarda ba sai da ya kafama malaman sharaɗi akanta. Sabbin matsaloli sun fara akan zuwan Mawaddat Islamiyya, dan bata karatun sai jibgar ƴaƴan jama’a, idan malami yay mata faɗa koya daketa koda akan karatu ne saita faɗama mahaifinsu, shiko ba kunya zai ɗebo ƴan sanda su kama malamin su rufe, wani lokacin ma har marin malaman yake da kansa. Yousuf ne da ya fahimci al’amarin na neman zama wani abu daban ya fara tsayawa akan tarbiyyar Mawaddat, dan ni ko kallon yarinyar na cikayi yanzu zaice itama ina son kashetane kamar uwarta. Dole duk yanda nake kwaɗayin janta jikina kodan maraicin mahaifiyarta da bata sani ba na haƙura na zuba ido dan a zauna lafiya. Dai-daita rayuwar yarinyar da Yousuf ke son yi ce yasa Isma’il ganin ɗan uwan nasa na takura mata. Dan haka ya tattarata ya ɗauke bayan gama Nursery school ɗinta ya maida ƙasar Garmany da zama. Ya ɗauka mata Nanny acan ƙasar aka sakata makaranta. Shima dai wasu harkokin kasuwanci da mahaifin Mawaddat ya sake ɗirasa akai ne yasa zamansa yafi ƙarfi a Garmany ɗin, ga kuma ƴar sonsa da ya maida can. Tafiyar Mawaddat babu jimawa na sake haihuwar yarona Namiji da yaci sunan Mubeen, bayan shi na sake ƴan biyu duk mata da gabonsu Suhaib sai auta Nazeer. Tunda aka ɗauke Mawaddat daga Nigeria bamu sake ganinta ba sai Yousuf dake zuwa akai-akai ganinta, dan shima Isma’il ya tsindumasa akan harkar kasuwancin kawo motocin da yake kanyi a yanzu, duk da dai kuma yana aikinsa anan ƙasar Nigeria saboda shine hubby nasa. Rayuwa ta shuɗa Isma’il ya sake bunƙasa haka ma Yousuf da yay aurensa, ya auri yarinyar kirki mai tarbiyya da sanin yakamata Saliha ɗiyar maƙwafcin nan namu da ya jagoranci bikina da Isma’il. Dan muna zaune lafiya kuma tana matuƙar girmamani. Mawaddat dai bata dawo ba, ko hutu bata taɓa zuwa ba har sai da ta kammala sakandare ɗinta a can sannan tazo mana. A halayen banzanta babu abinda ya canja sai ma ƙaruwa da yayi, dan yarinyar gaba ɗaya a fanɗare take babu wanda ya isa ya sakata ko ya hanata. Ko kallon banza kamata sai ta maida maka murtani, Yousuf ne kawai ke iya tsawatar mata ta nutsu. Hankalina ya tashi matuƙa, dan koba komai Mawaddat ɗiyar Isma’il ce, ita ɗin jininace ai koba aure tsakanina da shi. Dan haka na duƙufa da addu’a akanta kamar yanda nakema nawa yaran. Tawani ɓangaren kuma ina ɗan janta a jikina cikin hikima sai dai ban bata wata ƙofar da zata kawomin raini ba ko kaɗan. Kusan watanta shidda ta sake barin ƙasar zuwa London karatun ta na University, daga haka bata sake zuwa ba sai da ta kammala ta zama cikakkiyar lawyer. Da ƙyar daya ALLAHU Yousuf ya tilastata dawowa gida Nigeria, amma shi Daddynsu ko’a jikinsa. Dawowar tata kuma baisa abubuwa sun canja a yanda suke ba kanta a can baya tsakanina da Isma’il, dan ƙiri-ƙiri yake nuna bambanci tsakanin yarana da Mawaddat, idan nai magana yace arziƙin uwarta da Kakanta muke ci, dole na tattara na watsar da al’amarinsu, dan dama da ƙyar ya biyama su ƴan biyu kuɗin karatu zuwa Saudiyya, a yanzu haka kuma sun dawo suna aikinsu sai dai ba’a nan cikin Kano ba, shiyyasa sai Lokaci-lokaci suke zuwa mana weekend. Mubeen ne kawai tare damu sai ƴanmatana da da Suhaib da auta…..
Wannan kenan.
∆••••∆ ★∆••••∆
A ɓangaren su Uncle Smart da Lulu ƙamshi sun bar anguwar gaba ɗaya amma taƙi ta faɗa masa inda suka nufa. Shi kuma ya shareta ya cigaba da tafiyarsa a nutse. Yanda yake juya steering motar a nutse ya sata ɗan tsira masa ido a kaikaice. Sai dai ga duk wanda zai iya kallonta zai ɗauka hankalinta nakan tab ɗinta ne. Kamar wadda ta tuna wani abu kuma sai ta yamutse fuska da jan siririn tsaki ta maida hankalinta ga tab ɗin. Sunyi nisa sosai da anguwar dai-dai wasu gungun masu sai da kayan fruit ta ce, “Malam dakata min”.
Yanda tai maganar a gadarance ya sashi ɗan cizar lips ɗinsa. Ƙoƙarin wucewa yake ta sake maimaitawa cikin daka tsawa. Ƙin tsayawa yay sai da ya gota sosai ya gangara gefen titin ya kashe motar. Jitai wani irin tuƙuƙin baƙin ciki ya turniƙe mata zuciya har ta kasa yin magana ma. Sai huci take lips ɗinta na motsi amma ta kasa furta komai. Shiko ko’a kwalar rigarsa wayama ya ɗauka yana dannawa batare da ko kallonta sau ɗaya yayi ba.
“Amma kai babban illiterate ne!!”.
Ta faɗa cikin matsanancin ɓacin rai. Idan motar ta motsa to shima ya motsa ballema ya nuna mata yasan da shi take. Zata sake magana akai knocking glass ɗin motar, nan ɗin ma bai motsa ba, bai kuma sauke gilashin ba sai itace ta buɗe motar ta fita zuciyarta na mata wani irin tuƙuƙi, ji take bata taɓa tsanar wani mutum a duniya ba kamar wannan guy ɗin, dolene ma ta ɗauki mummunan mataki a kansa ta yanda ko ƙarar takalminta da warwarayen hanunta yaji sai hanjin cikinsa sun kaɗu………✍️
*_Ina bayanki ta wajenmu, karki bari ya raina ki😏, mutum sai ɗaukar kan tsiya aljihu babu manda🥱 gidan sanyi ma shiru ne. Bari nayi nan dan yau nasan namana ɗanye ga ƴan Smart team🚴😜🤪_*
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣6️⃣
………Wanda yay knocking glass ɗin ya gaisheta cikin girmamawa. Hannu kawai ta ɗaga masa. Bai damuba dan yasan halinta. Cikin yarensu na gayu ya ce, “Mi hajjaju ke buƙata?. Kankana, lemon zaƙi, abarba ko tuffa?”.
“Wanne gareku a ƙasa”.
“Duk akwai hajjaju, akwai ma sabon ɗiba daga lambu kuma sabon icce ne nata tsumayenki ko zaki shigo amma shiru”.
Karan farko hankalinsa ya ɗan fara komawa garesu. Kaɗan ya ƙara sauke gilashin motar yana kallonsu ta mirror. Muska taɗan yamutse da faɗin, “Daga wane garden aka kawoshi?, miye kuma tsaftarsa da ɗanɗanonsa?”.
“Hajjaju akwai sirri a ɗanɗano kam, gashi ya nuna luguf amma dai zan iya haɗa miki da shi kije kiga samfur”.
“Okay” kawai ta faɗa da miƙa masa kuɗi masu yawa da zasu iya kai naira dubu hamsin. Da sauri ya juya ita kuma ta buɗe motar ta zauna batare data rufeba ƙafafunta a waje. Shiko Smart cikin hikima ya cigaba da bin saurayin da kallo ta mirror da ya saita har yana iya hango wajen masu fruit ɗin. Yanda saurayin ya ɗanyi diri-diri zuwa ƙasan teburinsa kafin ya ɗago ya fara zuba fruit a ledan hanunsa ya sashi sake maida hankali garesa. Bai wani jimaba ya dawo da leda shaƙe da fruit. Ta ɗayan gefen ya zagaya ya ajiye gefenta, ita kuma ta shiga ta maida motar ta rufe. Ƙin taɗa motar yay har kusan minti ɗaya. Badai tace masa komai ba sai ma ƙoƙarin kai waya take a kunnenta.
“Kina shago ne?”.
Yaji ta faɗa batare da tayi sallama ba. Bai kuma san mi’akace mata da ga can ba ta dai katse wayar. Batare data kallesa ba ta faɗa masa inda zasu a taƙaice. Shima komai baice ba ya harba motar saman titi zuciyarsa na faman kai kawo. Lokaci zuwa lokacin yakan kalla ledar fruit ɗin ta cikin mirror. Sun ɗan samu huldup a hanya dan haka suka ɗan ɓata lokaci kafin suzo. Tun daga waje zaka san wajen saloon ɗin babba ne kuma na manyan mata masuji da manda a gidan sanyi. Ƙin fita tai ita a dole sai ya fito ya buɗe mata. Shiko ya shareta kamar bai fahimta ba. Aiki ta cika tai fam, dama ƙulle take da shi ta fara zazzaga masa masifa har mai saloon ɗin data kasance ƙawarta ta iso. Ita ta buɗe mata cike da murna tana faɗin, “Oyoyo my Lulu ƙamshi gawa taƙi rami” tai maganar tana jawo ganunta dole ta fito suka rungume juna. Suna niyyar barin wajen ta balla masa harara da jan tsaki tana faɗin, “Ka kuma jirani harna gama villager kawai Mtsowww”.
Idanu ƙawar tata ta wani tsira masa dan sai yanzu ta lura da shi. A hankali ta furta “Woow vary handsome fa, my Lulu Ina kika samo sa?”.
Harara ta balla mata da jan tsaki ta fisgi hanunta suka bar wajen. Itako sai ƙara waigowa take dan ba ƙaramin tafiya da imaninta Uncle Smart ɗin da tun kallo ɗaya da yay mata ta mirror ya ɗauke kai bai sake ba dan itama dai irin Lulu ɗin ce. Sanye take cikin skert da riga na atamfa sun masifar matsata kamar tai nishi su yage. Ga uban attachment kan yasha da zaro-zaro na farce da gashin idanu kamar ɗiyar aljanu. A dire take kuma ƙyaƙyƙyawace amma hakan baisa yaji ta ishesa kallo ba. Yanda take tafiya da waigensa yasa Lulu cikin takaici faɗin, “Wai ke Deeyah wace irin banzar yarinyace ban san kayan zubar da mutunci fa kema kin sani”.
“Wayyo my Lulu bazaki ganeba wlhy, Guy ɗin nan yay masifa-masifar haɗuwa dan ALLAH ina kika samosa?”.
“Mtowww! Ban sani ba banza kawai”.
Ta faɗa dai-dai suna shigewa cikin shagon saloon ɗin. Tuni yaran Nadeeya suka fara zubewa gaisheta dan sun san halin masifarta. Ko kallo basu isheta ba takai zaune a ɗaya daga kujerun saloon ɗin. Babu kowa a wajen sai Nadeeyar dama da yaran, dan duk randa Lulu zatazo gyara dokar da take sakawa kenan kar a amshi kowa bata buƙatar hayaniya da gwamutsen numfashi. Duk da hakan na tauye Nadeeyar haka take haƙuri tabi yanda take so dan a zauna lafiya. Amma kuma tana biyanta kuɗi sosai da yafi na aikin duk da itama Nadeeyar da ga babban gida ta fito, sai dai ko kama ƙafar kuɗin gidan su Lulu basuyi ba, su Lulun ma zasu iya kallonsu a faƙirai.
Nadeeya fa ta damu da son sanin wanene. Yayinda Lulu ta mata banza. Batai zuciya ba tama cikin yaranta sginal da ido. Fahimtar abinda take nufi da yarinyar tayi ya sata kaɗa mata kai. Cikin fakar idon Lulu ta ɗauka drinks da ruwa ta fita. Har yanzu yana zaune a motar ko buɗewa bai yiba, sai dai ya sauke gilashin tare da kwantar da kujerar yanda zaiji daɗi.
Ita kanta yarinyar sai da taji wani iri datai tozali da shi. Dan Uncle Smart ƙyaƙyƙyawan mutum ne kuma nutsatstse ɗan gaye ga masifar tsafta, irin mutanen nan ne masu shegen tsaftar shiya da a wajen wasu suke ɗaukar harma tai yawa, duk da baida kuɗi bai kuma tashi cikin dukiya ba ALLAH ya bashi lafiyayyen fata mai ɗaukar idon mai kallonsa ga kamala da cikar haiba. Rashin yawan walwalarsa da shiru-shiru na zame masa adon kwarjini ga duk wanda zai dubesa ko zama da shi. Cikin ɗan daburcewar harshe ta gaishesa. Hannu kawai ya ɗan ɗaga mata dan tunda yay mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Cikin ɗan in’ina ta ce, “Dama Aunty tace a kawo maka wannan”.
Kamar zai share sai kuma yay magana cikin deep voice ɗin nan nashi mai rikita marasa jin magana musamman ƙannensa, mai kuma saka ƴammata da yawa mutuwa a kansa, “Waye aunty?”. Cikin motsa lips ɗinsa a hankali.
(Masha ALLAH kaji wani dakakkiyar murya mai ratsa zuciya) ta faɗa a zuciya. A zahiri kam tai saurin faɗin, “Madam ɗinmu ƙawar aunty Lulu ƙamshi, Aunty Nadiy…..”
“Ba buƙata”.
Ya katseta cikin ɗauke kansa da lumshe idanu yamayi sama da gilashin gaba ɗaya. Tsaye tai sororo kamar kayan ado, sai kuma tabar wajen jiki a sanyaye. A cikin shago har an fara kwance ma Lulu kalbar kanta da wanke mata ƙafafu, yayinda suke hira da Nadeeya ƙasa-ƙasa. Sai dai hankalin Nadeeyar gaba ɗaya na kan ƙofa ne. Da mamaki tabi yarinyarta data dawo da abinda ta fita a hannu. Sai dai batace komai ba gudun kar Lulu ta ganota. Kusan mintuna biyar da barin yarinyar wajen ya buɗe idanunsa. Haka kawai zuciyarsa ke masa kaikawo akan ledar fruit ɗin nan. Duk da wani gefe na kwaɓarsa ya kasa hana kansa dubawa. Ɗakkota yay, ɗaya bayan ɗaya ya fara fidda fruit ɗin da aka loda a sama. Kamar yanda zuciyarsa ke raya masa acan ƙasa wasu abubuwa ne daban, fiddosu yay baki ɗayansu ya maida fruit ɗin ciki tare da ajiye ledar a inda ya ɗauka. Wani irin dokawa ƙirjinsa keyi da sauri-sauri ganin mugayen ƙwayoyin dake a ƙasan, kasancewar shi ba ma’abocin shaye-shayen bane babu abinda ya fahimta a tare da su, sai dai yasan dole ƙwayoyin zasu zama na shaye-shayen ne. Sake naɗesu yay da ƙyau ya adana acan ƙasa inda ƙafafunsa suke, da ga haka ya sake buɗe motar ya fiddo ƙafafunsa dan yasha iska.
Awani kusan huɗu Lulu ta kwashe a wajen gyaran jikin nan. Dan sai wajen 3 ta fito. Kallo ɗaya da yay mata sai da gabansa ya faɗi, yay saurin ɗaukewa yana jan siririn tsaki. Oho ita bama ta lura da shi ba. Dan yana da ga can gefe a bench na wani mai sai da ƙwa-ƙwa da aya da dabino dake ɗan jikin symbol ɗin shigowa harabar plaza ɗin. Tana da ga tsaye tana hararar motar da tunanin ko yana ciki amma shiru, a fusace ta fara knocking glass ɗin nan ma babu alamar za’a buɗe.
Ashar ta mulmulo cikin ƙufula da faɗin, “Mi wannan illiterate ɗin ke nufi da nine wai? Barin wajen yay ko mi?”.
“Kai haba shi ya fara wannan ganganci kamar bai san wacece Lulu ƙamshi ba ne”. Nadiya ta faɗa cikin ƙara fasa mata kai.
“Ai da alama har yanzu ban sanar da shi ɗin ba. Guy ɗin nan fa mara mutuncine da kike ganinsa. Na barshi ne ban koreshi ba tun a ranar farko saboda sai na gama wulaƙanta rayuwarsa sannan da nuna masa banbancin da ƙasa da sama ke da shi”.
Cikin ƴar dariya Nadiya ta sake faɗin, “Ai wannan karon drivern naki ne sam bai kama da driver ba wlhy. Irin wannan haɗuwa haka, da gani kuma akwai girman kai fa, koda yake ya kai yayi ne dan ya haɗu ba kary…..”
“Mtsowww kema shashasha ta biyu da har kika zauna masa kallo haka. Ina wani abin haɗuwa mutum na warin talauci da jahilci. Ƙaton banzar bana zaton (A) kota kai girman garinsu ya sani”.
Cikin dariya Nadeeya ta ce, “Kai Lulu harda sherinki, wannan ɗan ƙwalisar ne za’ace bai san miye A ba?. Da gani yayi karatu wlhy danni kamar ma na taɓa sanin fuskarsa a cikin ƴan ƙwallon Kano pillars sai dai nasan da wuya ace wancan ne”.
Tsaki Lulu ta sake ja cikin gatse ta ce, “Sai dai ƴan ƙwallon kwashe gotta ɗin anguwarsu. Dalla malama ni kin isheni”.
Nadeeya zata sake magana ya iso wajen, dan duk da ba jin mi suke faɗa yake ba da ga inda yake haka kawai zuciyarsa ke raya masa maganarsa suke, maganar kuma da bazata wuce zagi ya sha ba a wajen ƴar balaja’un tsagerar yarinyar nan. Wani banzan kallo Lulu ta watsa masa. Sai dai batace komai ba. Shima ɗin bai nuna yasan tana yi ba ya buɗe mata motar batare daya jira shigarta ba shi ya shige nasa mazauni………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣7️⃣
……..Sai da ta zagesa ciki-ciki da kalmar illiterate sannan ta shiga motar Nadeeya ta rufe da faɗin, “Sai mun haɗu anjima. Dan yau dole ne a warware gajiya Lulu ƙamshinmu ta samu lafiya. Barama na nemo Ɗan-takife ya haɗa mana kayan aiki yau network na gasken-gaske zamu hau”.
Yatsu biyu ta ɗaga mata tana murmushi, shi kuma yaja motar batare da bari ta faɗi abinda tai niyyar faɗa ba. Dama tun a kallo ɗaya da yayma Nadeeya ya fahimci itama tana shaye-shayen. Dan ita har jikinta ma ya fara nuna kansa saboda har taba tana sha. Masifar da batai masaba a farko ita ta fara zazzaga masa yanzu akan dan mi yasa zaija mota bata bashi iznini ba. Ko sau ɗaya bai nuna yasan ma tanai ba balle ya tanka. Hakan kuma na ƙara fusatata da cimata rai akan al’amarin sa, dan a duniya ta tsani tayi ma mutum abu ya mata shiru, amma shi kulatama bayayi balle ya bata haƙuri kamar yanda sauran masu aiki ƙarƙashinsu ke mata. Suna isa gida tun bai gama tsayawa ba ta fice a motar, cikin gargaɗi ta ce, “Sai nayi maganin wannan zafin kan naka baƙauye kawai”.
Da kallo kawai ya ɗan bita, sai kuma ya janye idanunsa yana ambaton auziyya saboda yanda skert ɗin yay mata ɗam illahirin surarta na juya kansu. Bayan ya kashe motar ya ɗan ja kusan mintuna biyu zaune shiru abubuwa da yawa na masa kai kawo, ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana mai cigaba da ambaton ALLAH tare da buɗe idanunsa dake lumshe har kalarsu ta canja. Ledar nan daya cire a fruit ɗinta ya ɗauka ya fito a motar, kai tsaye ya nufi wajen su maigadi. Suna cikin gaisawa Nazeer autan gidan ya fito. Sai da ya gaishesu dan sukam Mommy tsaye take akan tarbiyyarsu, bata yarda sun raina kowane ma’aikaci ba a gidan duk da wani lokacin su Hussaina kan so ɗaukar hallayar Lulu suce zasu taka ma’aikatan a bayan idonta. Duk kuma randa ALLAH yasa kunnenta yaji ko idonta yaji bata musu da wasa, shiyyasa ma suke shakkar aikatawar. Cikin ladabi Suhaib daya maida hankalinsa garesa ya ce, “Uncle Smart Aunty Lu ce tace na ɗauka leda a mota. Ta kuma ce wai karkaje ko ina yau har sai idan itace tace”.
Karan farko da al’amarinta ya so fara bashi dariya. Amma sai bai nuna ba ko’a fuska. Miƙewa kawai yay yaje ya Bama yaron ledar data aiko a ɗauka. Wadda ganin bai biyota da ita bane yasa ta fara masifa, da farko ma catai Suhaib ɗin ya kira mata shi, Mommy ce ta hana tace ya amso kayan kawai. Duk rashin mutuncinta tana jin shakkar Mommyn, dan haka ta cema Suhaib ɗin to ya faɗa masa yau kar yabar gidan nan sai da izinin ta. Kai kawai Mommy ta girgiza, a zuciyarta tana tausayin hallayar Mawaddat ɗin, dan tsaurin idonta da izza na bata tsoro. Koba komai ɗiya mace take, komai daɗewa ƙarƙashin ikon wani zata koma. Wanin ma da bata san shi kuma tashi kalar tsagerancin ba.
Koda Suhaib ya kai mata ledar fruit ɗin sama-sama kawai ta cire ta ajiye musu ta shige da sauran ɗakinta. Babu wanda yayi magana sai binta da sukai da kallo kawai. Duk da tana buƙatar wanka hankalinta ba’a can yake ba. Kayan shaye-shayenta kawai take buƙatar ɗan ɗorawa, dan kwana biyun nan da bata sha ba jinta take kamar mara laka a jiki, kuma kamar ana mata susa a brain. Tsaf ta gama zazzage kayan fruit ɗin a ƙasa batare data damu da yanda aka gyara ɗakin ƙal-ƙal ba. Duk da ba wani a cinkushe suke ba haka ta shiga tonawa da mamakin rashin ganin waccan ledar. Da gaske dai babu alamar ledar, dan haka ta miƙe zumbur, bataima kowa magana a falon ba ta fice. Har yanzu yana zaune a wajen su maigadi da sauran masu aikin gidan. Hira suke suna kwasar dariya shiko yana zaune shiru sai waya da yake dannawa, wani lokacin yakan ɗanyi murmushi da hirar tasu musamman idan sun sakosa a ciki. Cikin jan tsaki a zuciyarta ta ce, (Baƙauyen banza sai jin kan tsiya ko ubanwa zaima) dai-dai wajen motar da suka dawo ɗin ta dogare tana faɗin, “Kai!!”. Dukansu juyawa sukai suna kallonta. Shikam ko motsi ma baiyiba balle ya nuna yasan da zuwanta.
Baƙin ciki, takaici kamar zasu kashe Lulu. Cikin takaici da izza tace, “Wai kai banzan nan bada kai nake ba”. Yanzun ma shiru bai ɗago ba. Sai dai mai-wanki ya zunguresa da faɗin, “Aliyu da kaifa take inaga”.
Nan ma shiru yay yaƙi nuna yaji. Dan haka ta nufo wajen a fusace. “Wai kai mika ɗauki kanka? Waye ubanka a ƙasar nan?!!”.
Idanunsa ya ɗan rufe sai kuma ya buɗesu a hankali. Karan farko ya ɗagosu a buɗe gaba ɗaya ya zuba mata su. Wani irin motsawa zuciyarta tayi, dan wani irin kwarjini da shakkarsa ce ta daki ƙirjinta har zuciyarta na sukur-sukur a cikin jiki. Cikin ƙarfin hali ta watsa masa harara da faɗin, “Dalla malam daina kallona da wannan shegunayen idanun naka uwa na macizai”.
Bai janye idanun ba, haka kuma bai tanka mata ba dai, sai ma sake tsatstsareta yay da idanun duk da masifar da hakan ke haifar masa shi kansa. Neman daburcewa take, dan tama kasa cigaba da masifar da ke ta mata tuƙuƙi a zuciya. Fahimtar hakan da yay ya sashi motsa laɓɓansa karo na farko da nufin yin magana. Cikin deep voice ɗin nan tasa dake fita da dakewar da nutsuwar fitar da lafazi ya furta, “Duk macen data cika mace mai suturtawace akan kanta koda ga muharramanta ne, hakan kansa ko bata kira daraja gareta ba, darajar kanzo ta risina mata a gaban wanda ya fita ma balle wanda ke a ƙarƙashin ikonta. Wannan gata da musulunci yayma mace har a lafazinta ana so ta zama mai ƙyautatawa akan harshe”. Yana gama faɗa ya miƙe tare da miƙa ma mai-wanki dake kusa da shi key ɗin motar. “Mu kwana lafiya” ya faɗa cikin miƙa masu hannu ɗaya bayan ɗaya sannan ya nufi hanyar gate batare da ya sake ko kallon inda take tsaye ba.
Babu abinda ta fahimta a kalamansa, sai dai abin mamaki ta kasa koda motsa yatsanta garesa balle maida masa murtani ko yin masifa kamar yanda ta saba har ya fice gidan abin sai kace wani siddabaru.
“Aunty wani abu za’a ɗakko a motar?”.
Mai-wanki ya dawo da ita hayyacinta. Kamar wadda aka farkar a barci a zabure ta ce, “Ubanka zaka ɗakko min wawa kawai” ta juya zata bar wajen. Sai kuma ta dawo ta shiga nuna maigadi da yatsa. “Idan har kabar wancan ɗan iskan ya shigo gidannan a gobe a bakin aikinka kaima. Shima kuma ba ƙyalesa nayi ba, sai naga waye ubansa a garin nan, mi kuma yake taƙama da shi? Dan wlhy sai na wulaƙanta rayuwarsa ta yanda ko sunana yaji sai ya saki fitsari a wandonsa”.
(Ko kuma ke ki saki ba) mai-wanki ya faɗa ƙasa-ƙasa yana danne dariya. A zahiri kam kawunansu a ƙasa babu wanda ya motsa harta isa motar da suka dawo ta buɗe, ko’ina sai da ta leƙa amma babu alamar abinda take nema. Rai ɓace ta nufi komawa dan a zuciyarta ta fara bata *_Ƙwaro_* bai saka mata abubuwan nan bane. Dai-dai tana shigewa motar Uncle Yousuf nayin horn. Da sauri maigadi ya tashi ya buɗe gate ɗin. Fitowar Uncle Yousuf ɗin a motar shi da Smart ya sakasu sakin ajiyar zuciya a tare, a hankali mai-wanki ya saki dariyar da yake ta riƙewa tun ɗazun ganin Uncle Yousuf ya dawo da Uncle Smart ɗin tun ba’aje ko’ina ba. Hakan yasa mai bayin fulawoyi tayasa shima. Sai da sukai mai isarsu sannan mai-wanki ya ce, “Yau fa gamai maganin fitsararriyar nan. Ga kuma Alhaji ƙarami ya dawo da shi tun minti biyar basu cika ba, maga yaya wasan zai kaya. Dan wlhy ya mugun burgeni guy ɗin nan. Ga shi da alama ta tsorata da shi. Ai ban taɓa tunanin anan kusa za’a samu mai maganin masifaffiyar matar nan ba, sai gashi kuwa a cikin waɗanda tafi rainawa da cima zarafi wato mu ma’aikata, dan kawai muna neman guminmu a ƙarƙashin dukiyar gidansu sai take jin mune ƙasar takawarta a duniya”.
Nisawa maigadi dake kaiwa zaune yayi yana sakin wani ɗan murmushin manya. “Ai ni tun randa yaron nan ya fara zuwa nasan ba kanwar lasa bane ba, dan a cikin idanunsa zaka fahimci shima taƙadarin kansa ne”.
“Shine dai-dai da ita ai. Wulaƙancin yarinyar nan wanene bamu gani ba. Sau biyu fa tana marina”. Mai-wanki ya faɗa cikin ƙunar rai alamar har yanzu yana jin raɗaɗin marin a zuciyarsa, sai dai babu yanda zai yi…
Kafaɗarsa mai bayin fulawoyi ya dafa shima cikin ƙunar rai dan ya taɓa shan marin Lulun, “Ai ga mai rama mana nan yazo da ikon ALLAH. Fatanmu dai ALLAH yasa Alhaji Yousuf ya tsaya kan hanata korarsan da tace”.
“Ai insha ALLAHU bazata taɓa samun wannan damar ba ma. Dan randa ta dawo ashe shi aka aika ɗakkota tai masa halin nata yay tahowarsa ya barta acan, kamar dai yau ɗin nan da ya manna mata hauka, amma Alhaji Yousuf ɗin yaje ya dawo da shi aiki matsayin ma drivern ta, kaga ko da ace dane ai tun ranar zata koresa bayan taci masa zarafi kamar yanda takema na baya ko, kuma ya koru ɗin kenan. Nima a wajen Mubeen naji yana labartama yayansu Husain ta waya jiya”.
“Ai Alhaji ƙarami yana birgeni wlhy”. Cewar maigadi. Haka suka cigaba da gulmar Lulu da a gabanta to tari basu iyawa bare satar kallonta……….✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣8️⃣
………A ɓangaren Lulu kam sosai ta haukacema ƙwaro ta waya da masifa shiko ya dinga rantsuwar ya saka mata. Har abokinsa da yay komai a gabansa ya bama wayar ya zame masa sheda amma taƙi yarda. Sai ma katse kiran tai da tabbatar masa sai ya san ita ya cuta wlhy… Gado ta faɗa zuciyarta na mata wani irin tafasa, babu abinda ke mata kai kawo a rai irin maganganun drivern ta, haka kawai zuciyarta ke ingizata akan son sanin ma’anarsu. Wayarta data yasar gefe ta jawo. Nadeeya ta kira, ana ɗagawa daga can Nadiya ta fara da faɗin, “Bastie dama fa yanzu zan kiraki, dan gama wayata da Gajere kenan yace za’a samu kaya a wajen ogansa kona mil. ake s…..”
“Kinga ni ba wannan ba…”
Ta faɗa cikin katse Nadeeyar.
“Oh to ina saurarenki, na jiki kamarma cikin ɓacin rai, miya faru kuma? Badai driver ɗin ba kuma?”.
“Komai ma ya faru, har ma abinda banyi zaton faruwarsa ba ya faru. Wani Hausa nake son ki fassara min”.
“Tofa! Wane Hausa kuma?”.
Batasan ta haddace abinda ya faɗa matan ba sai da ta zayyanosu tsaf a yanda ya faɗesu babu ko gargada. _“Duk macen data cika mace mai suturtawace akan kanta har akan muharramanta, hakan kansa ko bata kira daraja gareta ba, darajar kanzo ta risina mata a gaban wanda ya fita ma balle wanda ke a ƙarƙashin ikonta. Wannan gata da musulunci yayma mace har a lafazinta ana so ta zama mai ƙyautatawa akan harshe”._
“Woow Madam irin wannan kalamai haka kamar wata mai tsara baitikan waƙe, dan ALLAH waya shiryasu haka….”
“Mtsoww malam dilla fassararsu nake buƙata nace”.
“Oh sorry, tab wlhy fa kalaman sunyi tsauri, ni kaina ban san yanda zan fassarasu ki gane ba dan hausan ba gama isata yay ba. Amma ina zuwa bari na tambaya”.
Tana ƙoƙarin ajiye wayar cikin jan tsaki Suhaib na mata knocking. “Uwar miye?”. Ta faɗa cikin masifa. Cikin tunzura baki Suhaib da ke da ga ƙofa dan bai shiga ba ma ya ce, “Uncle Yousuf ne yazo, ya ce kizo” da ga haka yay wucewarsa.
Tana son Uncle Yousuf matuƙa, tana kuma girmamashi saboda wasu dalilai nata na kanta. Dan haka tace ma Nadiya tana zuwa ta yanke wayar. Da mamaki mai nuna ɓacin rai take duban Smart da ke zaune a ƙayataccen falon nasu kusa da Uncle Yousuf. “Mi wannan abun yazo yimana nan Uncle You?”. Ta faɗa tana nuna Smart da ke zaune babu alamar ɗari-ɗarin nan irin na ma’aikaci da iyayen gidansa a tare da shi. “Ni na kirawoshi” Uncle Yousuf ya bata amsa cikin ɗaure fuska. “Uncle nifa bana buƙatar sake ganinsa” ta faɗa itama a harzuƙe.
“Da yay miki mi?”.
Baki ta tura gaba cikin kumbura fuska ta ce, “Wlhy na tsanesa, har ni wannan mutumin zai zaga. Korar ma da nai masa yanzu ba’ita kenan ba Uncle, ya jira hukuncin da zai biyo bayanta. Har ni zaima banza ina masa magana, sannan ya biyoni da baƙaƙen maganganu a gaban su maigadi, har shi waye? Mi yake jin kansa? Ɗan u……”
Hannu Uncle Yousuf ya ɗaga mata, “Ya isa haka. Mawaddat wai yaushe zakiyi hankali ne dan ALLAH. Yanzu abinda kike yi ko su Suhaib ƙannenki zasu aikata ne? Ke kullum cikin korar mutane. Yanzu dai ina son ki nutsu ki kwantar min da hankalinki, dan shiyyasa ma na dawo da shi gidan a yanzu dan na haɗu da shi a hanya ne. Ban kawo Aliyu gidan nan dan ki koresa ba, zan ƙara jaddada miki a yanzu shi ɗin zai dinga kaiki duk inda kike so dan saboda ke kaɗai ma na ɗaukesa aiki. Zai zo ƙarfe bakwai da rabi saboda takwas kike fita aiki, zai dawo da ke ƙarfe biyar da rabi kamar yanda kike dawowa shike nan ya tashi sai kuma washe gari period na gama magana.”
“Amma Uncle….”
Hannu ya ɗaga mata alamar baya buƙatar ta sake cewa komai, rai ɓace tabar wajen kamar zata fashe dan haushi. Da ga haka ya juya ga Smart da ke zaunensa a yanda ta shigo ta samesa batare da yabi takanta ba. “Wannan shine lokacin zuwanka aiki da tashin ka. Amma weekend zaka iya zuwa da ga goma zuwa huɗu sai ka tashi. Zan baka duka tsare-tsaren fitarta a rubuce, sai kuma idan zuwa wani waje ya kamata kasan aikinsu yana sakasu ɗan yinan-yinan koba shiri. Dan ALLAH ka ƙara hakuri, al’amarin Mawaddat sai addu’a, ga yanayin da take ciki na ƙara kangarar da ita. Kai tsakaninku ma akwai cigaba, dan naga alamar tana shakkar ka sosai”.
Karan farko ya saki ɗan murmushi da shafa kansa. “Alhaji wane tsoro kullum ana zageni da kirana illiterate ko villager. Kawai dai zanyi haƙuri domin mutuncinku da ceto rayuwarta, dan koba komai nima inada ƙanne mata, ina son kuma ALLAH ya karemin su a duk inda suka shiga.”
“Gaskiya ne wannan Aliyu. Ina godiya matuƙa a gareka da sake baka haƙurin di. Yanda ALLAH ya haɗa wannan zuminci a tsakaninmu ALLAH yasa muci moriyarsa har a gidan aljanna. Amma ina son naji wannan kalamai da aka faɗama yarinyata haka har suka harmutsa min ita, duk da nasan abu kaɗan ma fusata Mawaddat yake”.
Murmushi Smart ya sake yi a karo na biyu da faɗin, “A Alhaji ai ba’ayi haka ba. Tunda ya wuce a barsa kawai sai na gaba idan ALLAH yasa za’ayi a gabanka, duk da ina tsoron kuma karta kwaɗa min mari dan yau ma dai da ƙyar na sha shiyyasa ma na gudu”.
Dariya sosai Uncle Yousuf yake kwasa da faɗin, “A lallai ka tsira da ƙyar, dan a ma’aikatan gidan nan ɗai-ɗai ne basu sha marin Lulu ƙamshi ba kam”.
“To kaji ko Alhaji. Bara nayi nan kafin ta sake fusatowa ma, nasan yanzu bai zama lallai na sha ba”.
Dariya Uncle Yousuf ɗin ya sake kwashewa da shi, shi kuma ya fice yana ɗan murmushinsa mai sanyi, har ga ALLAH yana ganin mutunci da kimar Uncle Yousuf, yaji kuma zai iya haƙuri da yarinyar kodan shi ɗin. Mutum ne da yasan daraja da kimar mutane, duk yanda kake baya wulaƙantaka ko nuna maka ɗagawar shi ɗin wani ne. Ya iske har lokacin su maigadi na gulmar Lulu, ganinsa baisa kuma sun daina ba sai ma kwarzantashi da suka shigayi akan abinda yaymata. Komai baice musu ba sai kansa da ya ɗan girgiza kawai ya ciro wayarsa ya fara sana’ar tasa, ba kuma wani abu yake a ciki ba face game ɗin ball.
Bayan kamar awa ɗaya Uncle Yousuf ya fito zai wuce gida, Lulu ce tai masa rakkiya har wajen motarsa, aiko ta dinga antayama Smart da bai san tanayi ba harara. Dariya Uncle Yousuf ya dingayi ƙasa-ƙasa, dan sarai ya lura da ita, sai dai baice komai ba yayma su maigadi alheri kamar yanda ya saba. Godiya da addu’a suka shiga kwararo masa. Murmushi ya dinga musu kawai, dan harga ALLAH yana jin matuƙar daɗin addu’oi nan nasu. Duban Lulu da keta faman yamutse fuska yay, cikin tsokana ya ce, “To Daughter kin bani aron drivern naki ko na tafi da shi”.
Fuska ta sake kwaɓewa da faɗin, ni nama bar maka Uncle You, Dan bana buƙatarsa sai shegen girman kan tsiya”.
Dariya yayi, yana mai kiran Smart dake zaune kansa ke ƙasa. “Shiga muje” kawai yace masa. Bai musa ba ya raɓa ta gaban Lulu dake faman binsa da kallon banza, ciki-ciki ta furta, “An samu motocin banza sai hawa ake”.
“Ko ke kika zama mota hawa zanyi”. Ya faɗa shima a ƙasa-ƙasa lokacin da yake shigewa cikin motar.
“Kai ɗin banza! Shashasha!”
Ta faɗa a zafafe har tana zaburowa. Wani shegen murmushi ya sakar mata a karon farko yana ɗan ƙara gimtse fuskarsa kamar bashi ya furta ba ya shige motar abinsa. Wayyo ba’a taɓa Lulu ba ma ya aka ƙare balle. Dariya sosai Uncle Yousuf yake yi, dan ya fahimci akwai abinda ya faru duk da Smart ɗin ya fuske abinsa kamar bai aikata komai ba. Har yaja motar suka fice bata bar masifar ba.
“Na kula dai kai kake fara kunna min yarinya ka noƙe”. Uncle Yousuf dake dariyarsa har yanzu ya faɗa dai-dai yana harba motar saman lafiyayyen titin anguwar. Kaɗan Smart ya shafo kansa yana ɗan murmushi batare da yace komai ba. Sai da sukai ɗan nisa ya zaro ledar da ya cire a cikin kayan fruit ɗin Lulu. Buɗeta yay, tarin ƙwayoyi kala-kala suka bayyana. Motar neman ƙwacema Uncle Yousuf ɗin tayi, da sauri ya gangara gefen titi cikin rawar harshe ya furta, “Wannan fa Aliyu?”.
Cikin damuwa da ɓacin rai shima ya bashi amsa da, “Fitar da mukai ɗazun abinda muka fara tsayawa akai order kenan a wajen wasu masu fruits kafin mu ƙarasa inda tace zataje”.
Sosai jikin Uncle Yousuf ke rawa, dan har ga ALLAH shikam bawai bai yarda da maganar Doctor Khalifa bane, kawai dai rashin ganin al’amarin a zahirinsa ya sa bai kai masa ƙololuwa a rai ba, shiyyasa ma ya ɗora Smart ɗin dan ya samu tabbaci. Kamar wanda ya shiga ɗimuwa ya sake furta, “Aliyu Hydar! Ka tabbata a jikinta ka samu waɗan nan ƙwayoyin?”.
Cikin salon dakewar nan tasa da rashin son magana ya ɗan ɗage kafaɗunsa da faɗin, “Yaah! A gabana ma aka saya”.
“Dolene na saka a kama yaron nan dake sayar mata, bara ma na kira CP….”
Da sauri Smart ya dakatar da shi. “Niko a nawa shawaran Alhaji kamar kama yaron ba shine mafita ba tun a yanzu. Domin inaji a jikina ba dashi kaɗai take huɗɗa ba. Dan ka saka an kamashi kamar ka fargar da itane ta sake sabon salo ita da abokan mu’amalarta. Kaga kenan ba hanyar da zamu rabata da al’amarin muka ɗakko ba kenan, dan yanzu aka fara wasan kamar”.
Sosai maganarsa ta shigi Uncle Yousuf ɗin, dan haka ya ɗan dakata da ga ƙoƙarin kiran cp da yake shirin farawa, sai dai idanunsa sun kaɗa jazur harda ƴar guntuwar ƙwalla a cikinsu. Shiru babu wanda ya sake magana a motar har kusan mintuna huɗu, kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa.. Shine ya kashe shirun nasu da furzar da iska mai zafi. “Alhaji ni zan wuce, dan yamma nayi gashi ina son na isa gida da wuri”.
Cikin damuwa ya gyaɗa masa kai batare da ya iya furta komai ba har sai da ya fita yana ƙoƙarin rufe ƙofar motar ya kira shi a hankali. Ɗan duƙowa yay yana amsawa, Uncle Yousuf ya miƙa masa kuɗi masu yawa. Kansa ya girgiza da faɗin, “Kayi haƙuri Alhaji, tun farko na faɗa maka kada irin haka ya dinga shiga tsakaninmu. Hakkina kawai nake buƙata a kowane ƙarshen wata kamar yanda mukai alkawari. Na barka lafiya”.
Ajiyar zuciya mai ƙarfi Uncle Yousuf ya sauke ta re da sakin ɗan murmushi yana mai binsa da kallo. Tabbas a girme yasan zai iya bama Aliyun shekara bakwai. Amma dattako da kamunkan yaron na sakashi jin ya cika masa ido tamkar wani babba garesa. Wata irin kima da kwarjini yake masa a zuciya da cikin udanu. Yana matuƙar son ganin mutumin da yasan ciwon kansa a rayuwa da riƙe mutuncinsa. Ya yarda ya nema halak ɗinsa koda za’a kallesa a mai riƙe da sana’a mai ƙasƙanci, amma bai yarda ya ƙasƙantar da kansa ba wajen a bashi ya amsa balle zuciyarsa ta mutu. Insha ALLAHU zai taimaki rayuwarsa………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenku😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣9️⃣
……..Smart kam tuni ya shanye titin layin zuwa babban titi, da ƙyar ya samu napep. Tafiyar da bata wuce mintuna talatin ba ta kawosa anguwarsu. Kasancewar da sauran hasken gari koda ya shiga sai ya ɗan watsa ruwa tare da zuwa ya gaida Abba da su Ammah, sai dai ya iske Ammah ma ta fita ita da aunty Amarya Barkan ƙanwar Aunty Amaryar da ta haihu a can Gadon ƙaya tun la’asar, sai su Maryam kawai da suka dawo islamiyya. Dan haka bai zauna ba suna gama gaishesa ya fito ya koma ɗakinsa. Ba wasu abokai ne da shi ba shi dama sai Ahmad kuma ba anguwar yake ba. Dan Mutum ne mai ƙarancin kwaramniya. Idan kaga abokinsa da har zasu iya zaman doguwar hira to sai dai abokan karatunsa, amma na cikin anguwa sai gaisuwar mutunci kawai, duk da dai a da anyi abotar yarinta, sai dai kasancewar sa mara sakewa da mutane suke masa kallon mai girman kai duk suka janye jikinsu da shi, shi kuma bai nuna ya damu ba. Abokan karatun kuwa akan jima ma ba’a haɗu ba sai ta waya ko wani taro mai muhimmanci ya haɗa. Shiru ya kwanta kamar mai barci, da gani kasan duniyar tunani ya faɗa, dan babu abinda yake sai furzar da huci akai-akai da ga bakinsa, hakan kamar ɗabi’a ce data zame masa jiki in dai yana cikin damuwa.. Abubuwa ne masu yawa ke ci masa rai, ciki harda batun bauɗaɗɗiyar yarinyar can, shi mutum ne da baya shiga sabgar da ba tashi ba koda kuwa a cikin gidansu ne sai idan yaso, amma sai yake ji zuciyarsa na ingizashi akan taimakon ubangidan nasa da yarinyar, badan komai ba sai dan ƙannensa mata da bazai taɓa fatan su tsinta kansu a irin wannan rayuwar ba. Yasan idan har ya tsamota da ga wannan musifar yayi jihadi, sai dai bai san ta ina zai farama taro wannan al’amari nata ba. Karan farko yaja sirrin tsaki, sai kuma ya tashi zaune yana ɗan furzar da huci tare da kai hannunsa saman goshinsa yana ɗan murzawa. Ganin yaƙi samun nutsuwar hutawar da yake buƙata ya sashi tashi ya fito a ɗakin, nan ƙofar gidansu ya zauna yana ɗan gaisawa da mutane masu wucewa har akai kiran sallar magrib. Bai fito da ga massalacin ba sai da akai isha’i, yana kwaɗayin shiga gidan suyi hira da Ammah dan wannan ɗan lokacin kawai yake da damar haka gareta, amma zuciyarsa nata masa tuni akan Lulu da abinda yaji suna magana ita da ƙawarta zasuyi a daren na yau da sunan wai murnar samun lafiyarta. duk yanda yaso yaƙar zuciyarsa abin ya gagara, saboda yana ji a ransa ba alkairi za’a shuka ba wajen, dan haka ya fito da ga layinsu ya samu Napep zuwa hotoro gra. bai damu da kuɗin da suka tsuga masa ba. Ɗan nesa da gidan ya sauka, amma ya tsayar da mai napep ɗin, ya samu jikin wata bishiyar dabino kusa da katangarsu ya tsaya, ya kai mintuna talatin da wani abu a wajen yaji motsin an buɗe gate ɗin gidan, ido ya zuba na son ganin wanda zai fito. Ilai kuwa Lulu ce, dan a kanta idanunsa suka sauka saboda haske dake tako ina a street ɗin, gashi ta sauke glass ɗin motar sosai har kana iya hango kalar kayan da take sanye da su. Tayi ƙyau matuƙa ga uban ƙamshinta na isowa har inda yake tsaye saboda yanda ta gumbuɗashi kamar ba mace ba. A ɗan kasancewarsu na kwanaki ya fahimci sam bata tausayawa ƙamshi, haka kawai sai yaji tanan ɓangaren ta ɗan samu sassauci a garesa, duk da tana saka nata ƙamshi ne ba bisa ƙa’idar da ya kamata ace mace ta saka ba. Da sauri ya ƙarasa ga mai napep da ke zaman jiransa. “Kabi wannan motar Please, amma karka bari ta fahimci muna biye da ita”. Ya faɗa yana nuna ma mai napep ɗin motar Lulu da ke tafiya a hankali kamar bata son tuƙin yau. Yanda take tafiyar ya bama mai napep ɗin damar binta cikin hikima har zuwa wata sabuwar anguwa, dai-dai wani gida da alamu suka nuna shima ba’a daɗe da kammalashi ba ta tsaya, da ga inda suke yana hangen yanda ta kai waya a kunnenta alamar kira take ko an kirata, tana ajiye wayar ana buɗe gate ɗin gidan. Da sauri ya fita tare da miƙama mai napep kuɗi yana faɗin, “Abokina nagode ko”. Bai jira amsarsa ba ya nufi gidan, kasancewar akwai ƙarancin haske a anguwar dan kamar ma basu da wuta sai ƙarar gen… Ɗin gidan data shiga yake jiyowa ya samu damar bin motar tata ta gefe suka shiga tare batare da mai-gadin ya lura ba. Motoci ne kusan bakwai a gidan duk an parker a babban compound ɗin kamar wasu masu biki, tun kafin ta fito a motar ƙawayen nata suka baibayeta da ihun faɗin, “Sai Lu ɗin mu!!!, sai ƙamshin mu!!!”.
Fuskarta ƙawace da wani shegen murmushi ta fito. Wani shegen gown ne a jikin nata ta lafe mata kamar babyn roba. Da sauri ya kauda idanunsa yana mai jan sirrin tsaki da taune lips ɗinsa da ƙarfi. Bai sake kallon inda suke ba har suka shige ƙofar da yake ƙyautata zaton ta cikin gidan ce. Huci mai zafin gaske ya furzar tare da gyara tsaiwarsa. A ɓangaren su Lulu kam suna can cikin ƙaton falon gidan da ya sha kayan alatu. Abinda zai baka mamaki bawai iyakar su kaɗai bane ƴammatan ashe, akwai dattijan maza a shekaru bawai a cikar kamala ba har su huɗu, tun shigowar su Lulu kusan su duka suka zubo mata idanu fuska a washe, yayinda ita kuma nata murmushin ya ɗauke ta wani yamutse fuska tana kallon Nadiya, sai kuma ta juya ta fito a fusace. Da sauri Nadiya tabi bayanta tana faɗin, “Please Lu ki saurare ni.”
“Anƙi a saurareki ɗin, Nadiya kin san dai na tsani irin wannan ko…?”
“Na sani, amma bamu da wani zaɓi ne wlhy Lu.., dan ALLAH ki fahimce ni, kin san dai bazanyi abinda zai ɓata miki rai da gangan ba….”
“In ba kinyi da gangan ɗin ba miya kawo waɗan nan tsoffin banzar nan? Ni ban hanaki huɗɗa da su ba, amma ki sani duk randa suka zubar da ke bayan gama lalata miki ƙuruciya kiyi kukanki ke kaɗai kar ki tunkareni. Amma ki daina sakamin su a sabgogin rayuwata”.
Ɗan murmushi Nadiya tayi cikin rashin ɗaukar zancen na Lulu da muhimmanci ta ce, “Naji, ni dai yanzu kiyi haƙuri mu koma ciki dan ALLAH. Dan wannan fa zaman naki ne, dan ke akayisa, mun riga mun gama tara mutane, su Shony fa tun daga ktn suka taho a yammacin nan domin wannan shagali kawai. Abinda yasa ki ka ga su Alh. Baita anan ma saboda su Shony ne, dan sun riga sun kirasu cewar zasu shigo Kano, amma wlhy badan ke bane ba”.
A hankali ta furzar da iska, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya. “Shike nan amma ki kiyaye gaba, dan in har kika sake sakamin sabgar waɗan nan mutanen a tawa wlhy sai mun rabu. Suma su Shonyn idan suna buƙatar haɗuwa da su ne suje can su haɗu bai shafeni ba”.
“Naji na yarda baza’a sake ba. Suma kuma zan musu bayani yanda zasu gane Muje to dan ALLAH suna jiranmu”.
“Bani details ɗin mai kayan nan na tura masa kuɗinsa karna shiga wata sabgar. Sannan wannan gidan na waye uwar kwashe-kwashe kika kawo mu kuma?”.
Gidan Nadiya ta kalla tana ƴar dariya tare da faɗin, “Gidan wanda ya sayar mana da kayan ne, wlhy Guy ɗin akwai kirki gashi so handsome kuma, ya bamu shawara ne muzo nan musha shagalinmu dan zaifi mana sirri kasancewar kinga dare ne, ke kuma ba cika son shiga clubs na nan Kano kikai ba kin ce ƴan hayaniya da ƴan iska sun cika yawa”.
Cikin rashin damuwa ta ɗage kafaɗa kawai, batare da ta sake tofa komai ba ta bar wajen. Binta Nadiya tai suka shige tare…. Gaba ɗaya zuciyar Smart ta sake jagulewa da takaici, dan duk abinda Lulu da Nadiya ke tattaunawa yana jinsu batare da su sun lura da shi ba. Shigarsu da kusan mintuna uku sautin kiɗa ya fara tashi kaɗan-kaɗan saboda rufe windows da sukai duk dan kar kiɗan ya fita wa mutanen anguwa. Kansa ya ɗan dafe yana mai ambaton sunan ALLAH, gaba ɗaya ma ya rasa miya kamata yayi, duk da yazo nan ɗinne da burin ganin abokan sheɗanar tata da kuma hanata shan komai. To amma ta ina zai fara ma?. Ya kwashe kusan mintuna ashirin yana ƙullawa da kwance ta yanda zai shiga wajen…. Ƙarar hayaniya da ta fara tasowa kaɗan-kaɗan da ga cikin falon ta maidosa da ga dogon tunanin mafita da ya tafi, ajiyar zuciya yaja kamar wanda aka farkar da ga barci tare da tsurawa ƙofar idanu. Wasa-wasa hayaniyar ta daɗa karfi har yana iya shaida muryar Lulu saboda tsayawar ƙarar sautin kiɗan da ke tashi, da alama sun kashe ne ko wata matsala ta faru. Falon ya nufa da sauri batare da tunanin komai ba ko neman izinin ya tura ƙofar ya shige, yanda ya gansu a yamutse ga Lulu na ɗurama wani hamshaƙin Alhaji zagi har tanayi kamar zata tsole masa ido da ɗan yatsa ya sashi yin turus, mamaki ne ko takaici oho baima sani ba, kayan shaye-shayene da na ciye-ciye ko’ina a barbaje, yayinda alhazan nan guda huɗu da ya shaida fuskar biyu a cikinsu kasancewarsu wasu manyan ƙusoshin attajirai kuma ƴan siyasa masu faɗa aji a garin na kano ɗaya ke tsaye cikin fusata kamar zai daki Lulu, sauran ukun na zaune sun zuba mata ido harda wanda take zagin da shi fuskarsa ma ƙawace take da murmushi kamar bashi akema tujarar ba. Kalaman Lulu ne na ƙarshe-ƙarshe da kukan da ta fashe da shi ya dawo da shi hayyacinsa………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣0️⃣
……..Cikin kuka da dafe kanta tana ɗan layi alamar ta fara shiga maye ta ke faɗin, “Wlhy! Idan baka fita sabgata ba sai na keta maka rigar mutuncin tufafi da mutanen gari ke kallonka da shi, dan dama shi kaɗai ya saura gareka. Nace banayi! Banayi wai na minene wannan takura duk inda na saka ƙafa kana biye dani, shine yau harda bani wine saboda kai tsinanne ne, ka taɓa ganin na sha wine ne duk rashin ji na azzalumi!! Shin wai ku kuna ɗaukar duk macen da ke shan wannan abubuwan dan bama kanta farin ciki ita ɗin ƴar iska ce ko me? Manyan banza manyan kawai, ku gama hura hanci ga al’umma ku dawo bayan fage kuna lalata musu tarbiyyar yaransu. Ka sani har gaban abada bazaka taɓa samun wannan jikin ba, bama kai ba duk wani maye sai gani sai hange dan ni ba mazinaciya bace, bar ganin ina wannan rashin jin nasan ciwon kai na wawa kawai da ƙi ƙ…..” ta kasa ƙara sawa saboda shuuu da tai zata faɗi. Da sauri Nadiya ta tarota. Fisge jikinta tai tare da ɗagowa gaba ɗayanta kan ƙafafunta ta ɗauke fuskar Nadiya da mari haggu da dama.. A fusace Alhajin nan da ke tsaye tun ɗazun cikin ɓacin ran zagin da Lulu kema abokin nasa yayo kanta. Hannu ya ɗaga zai kwasheta da mari shima, sai dai cak ya tsaya jin an riƙe masa hannu ta baya. A karo na farko duk wanda ke’a falon ya farga da shi. Kallon ido cikin ido sukaima juna shi da Alhajin da ke faman huci. Idanu ya lumshe cikin girgiza kansa da faɗin, “Haba kai kuwa ai babba babba ne, ba’asan namiji kuma da faɗa da mace ba. Bakaga abokinka yanda ya nuna mazantaka ba? Tunda kun gama zubar da kimarku garesu banga abin tada jijiyar wuya ba idan irin haka ta taso a tsakaninku ai……”
“Kai kuma a matsayinka na ubanwa anan?”.
Maimakon amsa sai ya ƙara tsaresa da idanunsan nan masu kwarjini da suka gama ƙwarewa a kallo mai girgiza zuciya cikin nuna gargaɗi (Na macizai inji Lulu😂). Sakin hannun Alhajin yayi, kafin cikin yanayin nan nasa a daƙile da kowa ke ɗauka girman kai ya ɗage kafaɗunsa da ɗan taɓe lips ɗinsa. “Sanin ɗan waye ni bazai maka amfani ba, idan dani kake son sani sai na baka amsa da cewar drivern ta ne”.
“What?! Driver fa?!!. Ubanwa to ya baka damar shigo mana nan har da tsoma baki a cikin abinda bai shafeka ba?”.
Shi ba mai yawan magana bane, dan haka maimakon amsa masa a yanzun ma sai kawai ya zuba masa ido. Hon. HD Nakowa sai ya sake fusata. Magana zai sakeyi cikin fusata Alhaji Ɗan-kande Baita ya dakatar da shi.
“Kaga HD please it’s ok mana. Kai ɗan saurayi jeka kawai waje ka jirata nan ba huruminka bane ba”.
Wani banzan kallo Smart ya watsa musu su dukan, sai dai baice komai ba ya juya ga Lulu da ke zaune a kujera sharɓe tanata surutai da zagi har yanzu. Hanunta kawai ya fisga ta miƙe, batare da wani binta a hankali ba ya jata tana turjewa sukai waje. Da ƙyar ya iya kaita har motarta, dan haka ta maido da zagin da take ma Hon. Babale Misau kansa. Hakan bai damesa ba, sai ma rufeta da yay a motar ya koma falon ɗaukar handbag ɗin ta dan key ɗin motar na ciki….
“Ban yarda da wannan yaron driver bane ba, dan haka ina son a binciko min ɗan uban wanene shi a faɗin garin nan na kano”. Hon. HD Nakowa ne ke faɗa dai-dai Smart na sake shigowa falon ɗaukar tarkacen Lulu. Nunawa yay kamar baiji mi Hon. Nakowan ya faɗa ba, ya nufi handbag ɗin da ya gani ɗazun a hanunta da takalmanta masu azabar tsini ya kwashe ya sake juyawa ya bar falon ko kallo basu ishesa ba…..
Gotawarsu kaɗan da gidan wata dalleliyar mota ta iso ƙofar ita kuma. Horn yay aka buɗe masa. Yanda sautin kiɗa ke tashi a cikin motar zai baka tabbacin yana cikin nishaɗi matuƙa. Duk da yasan taro ake a gidan nasa hakan bai hanashi jin mamakin ganin wasu manya-manyan motoci guda uku ba, bawai ƴammatan bazasu iya zuwa da motocin bane, a’a kawai dai yasan sun musu girman da bazai yiwu ace sune suke hawansu ba. Cikin kai-kawo zuciya ya fito yana ƙara ƙarema motocin kallo, cikin ɗan basarwa irin na masu akwai ya ɗage kafaɗu da ɗan taɓe baki yay ciki abinsa ransa fal nishaɗi yau zai haɗu da mafarkinsa. Yayi alƙawarin sai ya ɗanɗani yarinyar nan dan ta tsare masa ko’ina na zuciya tun a randa ya ganta. Da wani irin sauri yaja birki ya tsaya yana ƙarema falon nasa da ya hargitse kallo, bawai na tarkacen da suka zube bane kawai dan yasan wannan ne ya kawosu ai. Iya shegen da ake aikatawa a falon duk da shima yasan yana aikatawa ya sashi zama turus, dan shi dai Nadiya batace masa zasu gayyato namiji ko ɗaya ba. Amma sai ga har mutum huɗu manyan mutane sa’ar Daddynsa, kai abinma tashin hankalin shine harda abokan Daddyn nasa ma da suka sanshi ya sansu. Da baya-baya ya koma ganin hankalinsu su bai kai kansa ba saboda shagala a ɓarnar da suke aikatawa da yaran mutane. Duk cikinsu baiga Lulu ba, gashi kuma an tabbatar masa da tazo wajen awa biyu baya da suka shuɗe. Waya ya ciro yay kiran Nadiya, an jima ba’a ɗauka ba dan har tana batun tsinkewa sannan aka ɗauka. Cikin wata irin murya ta ce, “Ranka ya daɗe barka da dare”. Sai da ya ɗan cije leɓen haushi kafin ya amsa mata da “Ta iso ne?”. Cikin muryar nan na wadda ta gama buguwa da shiga yanayin masha’a ta amsa masa da “Tazo amma shegen driver ɗin nan nata ya kwasheta sun tafi”.
“What!!” MM Atik Kumo ya faɗa da ƴar tsawa. Bai jira cewar Nadiya ba ya yanke wayar ransa a ɓace. Mota ya shige ya zauna tare da kwantar da kansa kan steering. A karo na biyu ya rasa damarsa akanta, tunda yake wata mace bata taɓa shiga ransa irin haka kamar yanda Lulu ƙamshi ta shiga ba. Da gaske sonta yake, yana kuma tsananin buƙatar mallakarta. Bai damu ace sai da aure ba, dan shi a halin yanzu babu maganar aure ma a gabansa duk da kullum faɗan momynsa kenan shine yay aure. Sai dai da to kawai yake amsa mata a duk sanda ta titsiyesa. Tun randa suka haɗu da Lulu a airport ya kasa hutawa da tunanin surar yarinyar da tsiwarta, burinsa kawai ya gusar da ƙishinsa gareta dan kowace mace tama daina birgesa a dalilinta yanzu. Sake kaiwa steering duka yay tare da tashi zaune yayma motar key a fusace ya bar gidan……
★★
Driving ɗin yake cikin ɓacin rai da takaici, yayinda ita kuma ta keta faman surutai da zaginsa akan ya maidata sai ta koyama Hon. Babale Misau da Nadiya da suka haɗa baki hankali. Faɗi take ita ba ƴar iska bace, duk wanda yace zai mata iskanci sai ta wulaƙanta shi…..
Wani irin baƙin ciki ne ya sake turniƙe zuciyar Smart dan surutanta sun ishesa, sake tunzura fushinsa suke zuciyarsa na ƙuna. Wani shegen birki ya taka a harzuƙe har sai da tai gaba ta bugu da kujerar gabanta ta sake buguwa da jikin ƙofa sannan ta koma ta zauna daɓar. Dafe kanta tai dan azaba kamar zata fasa kuka, sai kuma ta harzuƙo cikin fushi da masifa ga rashin kasancewa a hayyaci da ya ƙara hauhawar masifar tata ta ce, “Kai wai miyasa baƙauye ne akoda yaushe? Mugu so kake ka kasheni ka gudu da motan ko? Illiterate kawai, ba abinda ya iya sai shashashanci baƙauye”.
Idan motar nan ta motsa Smart to shima ya motsa, yakai matuƙar wuya so yake ya mata masifa dan maƙogwaronsa sai kaikawo ya ke a wuya amma yanata ƙoƙarin hana kansa, sai ma wayarsa da ya ɗauka ya fara danne-danne abinsa. Hakan ya sake fusata Lulu, da ma yaya lafiyar kura balle ta tsinke. Tana ƙalau ma yaya aka ƙare da jaraba balle yanzu da ya haɗa da maye. Sosai ta cigaba da zazzaga masa masifa ko haɗiyar yawu ma batayi, ganin badai zai kulata ba ta kama murfin ƙofar zata buɗe ta fita amma sai taji yayi lucking motar. Wayyo azabatun azaba. Yau dai kam yaga masifar ƙare dangi, dan bakinta baiyi shiru ba har sai da barci ya fara rinjayar mata idanu. Da wahala kaga Lulu tasha abu ya sakata barci, shiyyasa ko cikin abokanta ake ji da ita da kwarzanta ƙarfin kanta, amma yau da yake wani mugun haɗine MM Atik yay mata batare da ko Nadiya ta sani ba yasa abinda yafi ƙarfin kanta kala-kala wani ma bata taɓa shansa ba. Tun randa suka haɗu a airport bai huta ba, biye yake da ita yana ninƙaya cikin al’amurranta har sai da ya gama sanin ita ɗin wacece. Dan haka ya jawo Nadiya a jikinsa ya dinga jiƙata da kuɗaɗe harta amince da shi bawai yazo dan ya cutar da aminiyar tata bane son gaskiya yake mata. Ita da shi suka haɗa plan ɗin wannan phaty na samun lafiyarta, ya kuma saya musu duk kayan shaye-shayen tare da basu gidan hutawarsa da ya gama ginawa kwanan nan, shi yayi hakane dan ya rutsa Lulu a can, yayi imanin in har ya sameta sau ɗaya da kanta zata cigaba da nemansa kamar sauran ƴammatansa tana kawo masa kanta. Sai dai kuma kash, bayan ya gama wahalar haɗa dukkan plan ɗinsa wani shegen driver ɗinta ya zo ya rusa masa komai………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣1️⃣
……..Wayar da yake faman daƙila ya ajiye, dan dama yana dannawar ne kawai badan yana fahimtar komai ba da yake yi. Ta cikin mirror yake kallonta, sai kuma kamar wanda aka tsikara ya janye yana jan tsuki. Da sauri ya furzar da iska zuciyarsa tana masa kai-kawon tunanin ina ya dace ya dosa da ita. Gidansu ko gidan Uncle Yousuf?. A gidansu tana da ƙanne, kuma basu san halin da take ciki ba bayan iyayensu, ganinta a haka garesu zai ƙarasa zubar mata da mutunci ne a idonsu har ma da ma’aikatan gidan nasu da take takawa kamar ƙasa a duk sanda taso. Gidan Uncle Yousuf kam yaransa basu da wayo sosai kasancewarsu ƙanana, zai ma iya yiwuwa yanzu sunyi barci, ajiyar zuciya ya ɗan sake ja da kallonta ta mirrorn sai kuma ya janye idanunsa a lokaci ɗaya. Har ya ɗauki waya da nufin kiran Uncle Yousuf ɗin sai ya fasa, key yayma motar kawai ya cigaba da tafiya. Kaɗan-kaɗan sai ya dubeta ta mirror har suka iso gidan. Horn yay maigadi ya buɗe ƙofa ya fito, dan ba’ace masa wani zaizo gidan ba a irin wannan lokacin dan ƙarfe sha ɗaya saura. Ƙarasowa yay jikin motar sosai, Smart dake kallonsa shima yay ɗan murmushi da faɗin “Baba Barka da dare yaya aikin?”.
Murmushi shima maigadi yayi, dan ya ganesa. Cike da kulawa ya ce, “Mazan fama kaine yanzu da dare haka?”.
“Eh baba na kawo wannan ne”. Yay maganar yana nuna baya, ɗan leƙawa baba maigadin yayi, ganin Lulu kwance a bayan ya sashi ɗan yin baya yana dafe baki dan shi a zatonsa ko barcin isa ne take yi. Da sauri ya koma ciki ya buɗe gate ɗin. Har gaban ƙofar shiga falon gidan Smart yay parking. Sai da ya kashe motar ya fito sannan ya ɗaga waya ya kira Uncle Yousuf. Ba’a jima ba aka ɗauka. Shi ya fara gaidashi dan a girme dai ya girmesa. Uncle Yousuf ya amsa da ƴar fargaba, sai yay saurin tambayarsa badai wani abu ya sake haɗasa da Mawaddat ba?.
“A’a Alhaji komai bai faru ba. Itace dai na kawo nan ɗin gamu a ƙofar falo”.
Da mamaki Uncle Yousuf ya miƙe zumbur, Jallabiyarsa ya ɗauka ya zura dan har sun kwanta ma. Ko amsa tambayar lafiya da Aunty Saliha ke masa baiyi ba ya fice cikin sassarfa yana faɗin, “Ina zuwa”. Shi da kansa ya buɗe motar ya leƙa, ƙirjinsa yay matuƙar bugawa, ɗagowa yay yana kallon Smart kallo na neman ƙarin bayani. Fahimtar hakan shi kuma ya sashi furzar da iska kaɗan. “Bayan tafiyata ta fita, jin hirarsu da ƙawarta a ɗazun ya sani sake dawowa, sai na samu zata fita shine na bita”.
“Ya Arrahaman harma ta sha kenan?”. Uncle Yousuf ya faɗa cikin matsanancin damuwa.
Tausayi sosai ya bama Smart, ya ɗan cije lips da faɗin, tana buƙatar saka ido sosai dan koba wannan halayyar bai dace ace mace kamarta tana fitar dare ba haka Alhaji”.
“Gaskiya ka faɗa Aliyu, na kuma gode sosai da ƙoƙarinka, duk laifin na yaya ne da bazai iya tsawata mata ba a duk sanda yaga zatai fitar, amma inasha ALLAH zan ɗauki mataki ni da kaina. Sai dai abin damuwar nima ɗin wani lokacin bana nan tunda ina tafiye-tafiye, da zaka min alfarmar dawowa kusa da mu da naso haka Aliyu, wlhy na yarda da kai, ina jinka tamkar ɗan uwana na jini, zan iya bar maka amanar Mawaddat batare da jin ko ɗar ba a zuciyata….”
“Nagode sosai da wannan karamci Alhaji. Sai dai maganar dawowa nan kam abun ne mai wahala gareni, dan Abba ma bazai yarda ba balle kuma Ammah. Sannan nima inada ƙanne, kuma suna buƙatar saka ido duk da dai ba wayona ke tsaremin su ba ko jajircewa. ALLAH ne gafurin rahimun”.
Duk da Uncle Yousuf ya gamsu da bayanin nasa amma bai so hakan ba. Dan yana matuƙar buƙatarsa tare da su. Yaron nada wata nagarta mai matuƙar ƙayatarwa. Ga nutsuwa da cikar kamala tamkar ba talaka ba. Godiya yay masa tare da fiddo Lulu da ke sharɓan tana ɗan surutanta jefi-jefi a cikin barcin, wanda ba komai bane sai zagin Hon. Baita. Shi dai sallama yay masa zai wuce. Dakatar da shi yay da faɗin, “Kaga dare yayi yanzun. Kaje da motar gida dan abin hawa zai iya maka wahala”.
Kamar zai ce a’a sai kuma ya tuna maganar Uncle Yousuf ɗin gaskiya ce. Dan haka ya gyaɗa kansa tare da godiya. Saida ya ga ya shige ciki sannan shima ya shiga motar ya tayar ya bar gidan. Mubarak kawai ya samu a waje alamar dai shi ake jira, cikin washe baki Mubarak ɗin ya taso yana masa sannu da zuwa da shafa motar har ya kasheta ya fito yana lucking. “Yaya ka sayi mota ne?”. Mubarak ɗin ya faɗa cikin zumuɗi. Karan farko yayma yaron ɗan murmushi. Cikin deep voice ɗin nan tashi da ta gaurayu da gajiyar son yin barci ya ce, “Daga ganin sarkin fawa sai miya tai zaƙi Mubarak? Ta mutane ce”. Kamar an zarema Mubarak lakar jiki ya ɗan rausayar masa da kai gefe kawai. Daga haka suka shige ciki gidan shiru alamar duk anyi barci, sai wasu a ƴammatan dake waya da samarinsu, idan ka cire Asma’u da Maryam dako wayar Yayansu yama hanasu riƙewa sai ta Ammah suke ɗan ɗauka. Ɗaki kawai ya shige dan kwanciya yake matuƙar buƙata…….
★★★ ∆∆ ★★★
Da asuba Uncle Yousuf da kansa ya shiga ɗakin aunty Saliha da ya kai Lulu dan ita a ɗakinsa ta kwana ya tadata yin salla. Sam bata da nauyin barci, damma yau akwai na maye tare da ita, da alama kuma ya bugar da ita da yawa, dan ma tana da jini mai ƙarfi, da ace tana da saurin buguwa ma abubuwan da MM Atik Kumo ya harmutsa mata zata iya ƙara shanye yinin yau bata san inda kanta yake ba. Amma sai gashi Alhamdullah ita da sauƙi ya saketa. Zata fara masa gardama ya daka mata tsawa. A firgice ta tashi zaune zumbur jin Muryar Uncle Yousuf tana mazurai. Sosai take zazzaro idanun mamaki, shiko ya watsa mata harara da faɗin, “Karna dawo Massalaci na tadda baki tashi kinyi salla ba, zan matuƙar ɓata miki rai”. Kai kawai ta gyaɗa masa mamaki fal ranta akan ganinta nan ɗin. Sai kuma abinda ya faru a daren jiya ya shiga dawo mata ɗaya bayan ɗaya. Cikin wani irin takaici da jin ƙuna a rai ta dafe kanta tana jan tsaki. A fili ta furta, “Sai nayi maganinka wlhy, illiterate kawai ko wa yace ya kawoni nan? To wai ubanwa ma ya nuna masa can ɗin da har ya bini?” Anya mutumin nan baida iskoki bisa kai ko? To inba mai iskoki ba itako mizata kirashi? A jiya dai tasan ya tashi a aiki ai da wuri ma. Amma kuma sai gashi ta gansa a inda babu wani mahaluki da yasan zataje. Kai wannan lamari da mamaki, dole ne tasan yanda ma akai ya bita can, kuma sai ta koya masa hankali akan shiga abinda bai shafesa ba. Nadiya ma sai ta shuka mata rashin mutuncin da bazata taɓa mantawa da shi ba da ga ita har su Hon. Baita ɗin. Jin ana neman idar da salla ya sata sauka a gadon dan tasan Uncle Yousuf babu wasa ne, ba ruwansa rufe ido zaiyi yaci mata uwa babu ruwansa da shirin da sukeyi. Wanka ta farayi sannan ta ɗauro towel Dan tana so ta sake wattsakewa. Batako zaman jiran tsanewar jikinta ba ta zura abayar Aunty Saliha. Sallar tai babu wani nutsuwar a cikinta, tana zaune a inda ta idar tana kulla mai fishseta Uncle Yousuf ya leƙo, gaidashi tayi, sama-sama ya amsa mata duk da yaga yanda ta koma kalar tausayi. Ba yanzu ya shirya mata magana ba dan haka yay ficewarsa. Ji Lulu tai gaba ɗaya hankalinta ya gama tashi, sam bata ƙaunar fushin Uncle You a rayuwarta, har gara ma Daddy yay fushi da ita dan shi tasan abu ɗaya zata masa ya rikice ya dawo lallaɓata. Kuka take so tayi, sai dai ita mai juriya ce da shegen taurin kai, ba a komai take iya kuka ba komai ƙololuwar ɓacin rai ko tashin hankali da zata tsinta kanta a ciki. A karan farko taji kunyar haɗuwa da mutanen gidan, tashi tai jikinta duk babu ƙarfi, bata ko nemi jakarta da takalminta ba ta fice cikin sanɗa, taji daɗin rashin samun kowa kuwa, da sauri tabi ta ƙofar kitchen ta baya. Tunda ta fito bayin fulawoyi ke mata kallon mamaki da ga nesa, dan shi dai bai san sanda tazo gidan ba kam, ƴar tsawar da tai masa ta sakashi dawowa a hayyacinsa. “Wawa mi kake kallo ne? Dilla buɗe min ƙofa!!”. Jikinsa har kakkarwa yake duk da kuwa a girme ma zai iya girmarta shima, kuma ba aikinsa bane, ta watsa masa harara lokacin da take ficewa tare da jan tsaki. Yasan laifinsa dan haka ma baiji haushi ba. Mawaddat ta tsani taga ana kallonta, gashi kuma yau shi ta kamasa dumu-dumu. Ya san dai bala’i bai ƙare ba, dan duk randa ta dawo gidan zai sha masifa. Ƙila ma harda zagin ƙare dangi za’a haɗa masa.
Da ƙafa ta isa gida, kasancewar garin da sauran duhu ga ɗan sanyi-sanyin da aka fara na lokacinsa. Acan ma sai da maigadinsu ya samu rabonsa na zagi. Dan shima dai galala yay yana mata kallon mamaki. Amma tunda ta fara danna masa na maguzawa sai ya nutsu ya koma gaisheta a daburce. Bata amsa ba tai shigewarta tana jan tsaki……….✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣2️⃣
……..Anan kam tasan basa barin ƙofa a buɗe, dan haka ta zagaya ta window ɗin ɗakin Iya Tabawa. Tana kuwa zaune tana addu’oi tun bayan idar da salla. Ba yau Lulu ta fara mata haka ba, shiyyasa koda ta kirata bata firgita ba. Sai ma miƙewa da tai a ɗan ɗarare. A kausashe Lulun ta ce, “Dalla Malama ki buɗen ƙofa kin wani tsaya kallo na”. Haƙuri Iya Tabawa ta bata ranta fal wasi-wasi. Zuciyarta ta fara raya mata ko dai yawon banza Lulu ke fita ne, tunda ba taɓa ganinta cikin maye tai ba. A ƙasar Hausa kam mafi yawan al’umma sukan fassara yawon dare na ɗiya mace da tazubar ne kawai, da wahala hasashensu ya wuce haka har su hango wasu abubuwa masu illa a rayuwar ƴaƴanmu mata bawai zina kawai ba. Sun manta a rashin ji duk abinda namiji yasa kansa iyawa wasu matan kan kwatantashi ba wai sai iskanci kawai ba. (Ya rabbi ka shiryar damu da zuri’armu baki ɗaya).
Tana shiga ɗakinta a saman katafaren gadonta ta zube tana mai sauke numfashi, lamo tai cikin lallausan bedsheet da duvet ɗin gadon masu ltaushin tsiya da ƙamshi. Tunanin matakin da zata ɗauka akan tsageran driver ɗinta takeyi, da su Hon. Nakowa, sai dai kuma barcin da bai gama fita idonta ba ne yaci ƙarfinta……
★Kasancewar alerm data saita ƙarfe takwas ta farka badan barcin ya isheta ba. Sai dan tana da shari’a mai zafi a yau ɗin da zata gudanar wadda a yau ɗin take fatan alƙali ya yanke hukuncinta. Cikin rashin kuzari ta tashi ta faɗa toilet, sai da ta gamsu da gyara jikin nata a fannin wanka sannan ta fito. Shiri tayi tsaf da ita cikin suit na mata kalar baby pink, rigar cikinta fara. Dan ƙyau kam tayi ƙyau, ga shegun takalmanta masu dogayen dudduge ɗin nan da tsabar ƙwarewa a sakasu yasa ko gargada batayi a tafiya da su. Yau dai anyi abun arziƙin saka ƙaramin baby hijab fari da yay mata ƙyau sosai, sai dai iyakarsa kafaɗarta dan ƙaramine. Ƙamshin nata na fitar hankali ta bulbula a jiki har ita da kanta tanajin ƙamshin na hawa mata kai, sai dai haka take buƙatarsa. Cikin takun nan nata na isa da gadara ta fito, illahirin jikin nan na motsa kansa kamar wata tarwaɗa a ruwa. Mubeen kawai da Daddy ta samu a dining suna breakfast, sai Mommy tana tsaye a tsakkiyarsu da alama abincin take haɗa musu.
“Good morning Daddy & Mommy!”. Ta faɗa kanta tsaye babu wani alamar respect gareta matsayinsu na iyayenta. Musamman ma Daddy dake amsa sunan mahaifi. Kowa dai yasan yanda ƴaƴa ke shakkar iyayensu maza fiye da mata a ƙasar hausa. Mommy dai kallonta kawai tai ta girgiza kanta. Shiko Daddy fuskarsa a washe da murmushi, duk da dai kamar alamunsa na nuna yana cikin damuwa ne yake dannewa.
“Morning sweet heart. Kin tashi lafiya? Yaya ƙarfin jiki”.
“Komai normal Daddy”. Ta faɗa tana ɗaukar shayin gabansa da yake sha ta kurɓa da ga tsayen da take. Da kallo ya bita har yanzu da murmushi a fuskarsa. “Babyna zauna mana kisha ba ƙyau shan abu da ga tsaye ai”.
“No Daddy, hakan ma it’s ok for me. Ina sauri ne 9:30 inada Shari’a”.
“Allah yay miki albarka, ya kare munke ga duk wani sharrin maƙiya na gida dana waje”.
“Amin sweet Papa na”.
Sarai Mommy ta fahimci harda ita a addu’ar tasu. Hakama Mubeen. Dan tuni sun gane abinda mahaifin nasu kema Mommy akan ƴar uwarsu. Sai dai ko sunce zasu ɗauki mataki hanasu yin hakan Mommyn take yi. Babu yanda suka iya dole suke haƙura. Amma badan jajircewarta a kansu ba ba ƙaramar tsanar Lulu sukeji ba a rai. Wani lokacin ma hatta shi Daddy ɗin takaici yake basu shiyyasa su ƴan biyu sam basu son zaman gidan. Harta ɗan sha shayin na Daddy kusan sau bakwai ta ajiye Mubeen bai mata magana ba itama batai masan ba. Batama nuna tasan da zamansa a wajen ba kamar yanda shima ya nuna. Tana shirin sauka a ɗan steps ɗin hawa dining ɗin Daddy ya dakawa Mubeen ɗin tsawa.
“Kai dan uwarka ita ɗin sa’arka ce da bazaka gaishe ta ba?!”.
Kallon Daddy ɗin Mubeen keyi zuciyarsa a bushe, sai kuma yaja numfashi mai nuna zuciyarsa na yunƙurowa, sai dai kallon gargaɗi da Mommy ke masa ya hanashi cewa komai da ga tarin abubuwan faɗar da ke cikin bakinsa game da mahaifin nasu. A hankali ya furta “Daddy kayi haƙuri” kawai yaja bakinsa ya tsuke.
Tsaki daddy yaja dai-dai Lulu na ficewa a falon gaba ɗaya. Bata jira jin abinda Daddyn ke shirin faɗa ba. Karo na farko a rayuwarta taji kamar babu daɗi akan abinda Daddy ɗin kema ƴan uwanta saboda ita. Har ga ALLAH tana ƙaunar ƴan uwanta, hasalima bata haɗa son su da komai ba. Hatta su Yaya Hassan batajin daɗin rayuwar doya da manjan da ke a tsakaninsu. Dan ko gidan su ƴan biyun sukazo basa kulata bata kulasu, saboda sun riƙe abubuwan da mahaifiyarsu ta fuskanta da ga mahaifinsu dalilin mahaifiyarta da ita kanta. Goshinta da yay mata nauyi saboda abinda ta sha jiya bai gama sakinta da ƙyau ba ta ɗan shafo tana furzar da iska. Ba ƴan uwanta kaɗai ba hatta Mommy tana jin ƙaunarta, dan kallon uwa take mata a zahiri da baɗinin rayuwa. Ta sani duk wanda yasan gidansu ma ya sani Mommy bata taɓa cutar da rayuwarta ba koda da harara, idan dai tayi laifi yanda take ma yaranta faɗa itama haka take mata. Shiyyasa duk rashin mutuncinta har abada bazata taɓa kwatantashi ga Mommy ɗin ba. Musamman ma idan ta tuna nasihar da Kakanta Alh. Sufi Garko kanyi mata a duk sanda taje garesa game da Mommy ɗin da halaccinta ga zamantakewarta da mahaifiyarta. Duk da dai itafa har yanzu bata taba jin labarin ainahin zaman da Mamanta tayi da Mommy ɗin ba…… Gaisuwar da ma’aikatan gidan ke mata ce ta katse mata tunani, batare data kalli ko guda a cikinsu ba take wucewarta kawai da takun nan nata na yauƙi da isa. Tana gab da isa motar da take buƙatar hawa idanunta suka sauka akan Smart da ke zaune wajen maigadi kamar kullum hankalinsa a waya yana buga game ɗin ball da yake matuƙar bege. Sake tamke fuska tai da ɗauke kanta, abinda ya faru jiya ne ya shiga mata kaikawo cikin kai. Sosai taji ɓacin rai ya sake baibayeta da takaicin su Nadiya da suke son jamata rainin nan wajen wannan shashashan, ta jima tana shaye-shaye, amma duk wanda yay mata sani na haƙiƙa bai san wannan halayyar tata ba, a koda yaushe cikin ƙoƙarin binne sirrinta take, amma sai gashi a haɗuwarta da mutumin da tafi tsana fiye da kowa a duniya shi ya ganta a yanayin. Ƙwafa tai da balla masa harara, cikin borin kunya ta cilla masa key da sake jan tsaki. Idanunsa da ke nuna alamun barci bai ishesa ba ya ɗan lumshe ya sake buɗewa, batare da ya kalleta ba ya miƙe zuwa gaban Motar data ɗakkoma key ya buɗe mata bayan, sai da ta shiga ya maida ya rufe sannan ya koma mazaunin driver, motace mai tsadar gaske da ɗaukar hankali, kasancewarta ƴar gatan gidan hatta Daddy tafi yawan motoci. Dan motarta biyar kuma duk ƙosassu, sai ƙarama ɗaya da sha’awa kawai ya sata matsawa Uncle ɗinta Khamil ɗan uwan mahaifiyarta dake Abuja saya mata ita. Dai-dai suna barin kan titin layin nasu ya miƙa mata handbag ɗinta ta jiya da key ɗin mota, a hankali ta ɗago da ga duba takardun da takeyi ta ɗan sake hararsa sannan ta kalla kayan a yamutse. Murya a dake sai dai acan ƙasan maƙoshi ta furta, “Waya gayyaceka inda nake jiya?”.
Sarai ya jita, amma sai yay kunnen uwar shegu da ita ya haura kan babban titin bayan motar da ya dakatama ta shige layin da ya fito. “Malam da kai nake yi”. Ta sake faɗa cikin zafin rai da borin kunya. Karan farko ya ɗan ɗago idanu ta cikin mirror ya dubeta. Ido suka haɗa, tai saurin kauda nata zuziyarta na tsirgawa. Itafa komi za’ai ayi amma kar ya kalleta da wannan shegun idanun na macizai (kamar yanda ta raɗa musu😂🥱). Yanda tai ɗin sai ya so bashi dariya, amma sai baiyi ba ya ɗan saki murmushin gefen baki da maida hankalinsa ga titi cikin salon lumshe idanun nasa kamar yasan suke razanata, babu alamar zai bata amsar da take buƙatar son ji. Ba ƙaramin takaicinsa bane ya kume Lulu, ga wayarta ta isheta da ruri. Nadiya ce keta faman kiranta tun ɗazun, sai dai taƙi ɗagawa dan tai alƙawarin sai ta koyama ƙawar tata mafi kusanci hankali. Tsaki taja a karo na babu adadi, ta fisgi wayar da ke kan rigarta ta lauyoyi ta kashe tare da sake cillar da ita kan rigar da ke a gefenta. Haushin Nadiyar dana sharetan da yay ta tattaro gaba ɗaya ta nufesa da shi.
“Wai kai mika ɗauki kanka ne da har ina maka magana kana wani cika da batsewa?”.
Yanda tai maganar muryarta har tana zuga kamar wadda kuka ke son yunƙuromawa sai dai ƙarfin halinta na dannesa ya sashi sake dubanta a karo na biyu ta cikin mirrorn. Sake maida kansa yay ga titin sai kuma ya ɗan muskuta zamansa da furzar da iska. Ƙasa-ƙasa na rashin kuzarin da kasala irin na wanda barcin bai ishesa ba cikin deep voice ɗin nan ta shi ya ce, “Mi kike son sani?”.
Wata irin kasala muryar tasa ta nema saukar mata saboda yanda yay maganar cikin sanyi da tausasa lafazi, sai dai cikin yaƙi da kai da nuna juriya irin ta masifaffun mutane ta watsa masa kallon banza da yin ƙwafa tana maida kanta ga takardun da take dubawar. Kamar bazata ce komai ba sai kuma bayan kusan minti ɗaya ta ce………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣3️⃣
………“Waya aike ka inda ka sameni jiya? Miye ma dalilinka na bina?”.
Idanu ya lumshe tare da buɗewa a lokaci guda. Kamar yanda yay magana ɗazun a tausashe yanzu ma haka yayi. “Baki so asan kina aikata abinda na gano ɗin ne?”.
“Kai ɗin banza da zanji ina son ɓoye maka abu. Shiga abinda ban saka ka bane ya sa nake neman ba’asi dan bana son shiga sharo. Idan kuma kace zaka cigaba da shiga min hanci wlhy zan saka ka dana sani kai da duk wanda ma yake maka kallon arziki. Tsabar kai ɗan haɗin masifa ne ka ɗauke ni ka kai gidan Uncle you.., wlhy kasan mima zaka faɗa masa, in ba haka ba sai naje har gidanku kaima na maka ƙullin da har gaban abada baka isa ka kwancesa ba ɗan sa ido kawai. Idan kuma kaji ƙarya mu zuba ni da kai mai shishshigin tsiya, kai a dole sai ka shiga jikin iyayena dan maular tsiya irin ta talaka”.
(Maula! Talaka!) Zuciyarsa ta maimaita cikin jin ƙunar kalmomin. Kamar zai yi magana sai kuma ya haɗiye abinsa dan ya fahimci al’amarinta na buƙatar sai da uzuri, idan yace zai biye mata sai ma su zama ɗaya. Yanda bata sake magana ba tana ta faman duba takardun nata shima bai sake kallon inda take ba, sai dai ƙamshin turaren data bulbula ya addabesa har yana hawar masa kai kamar yanda itama nashi ke cizon can ƙasan zuciyarta. A cikin tsare-tsaren da Uncle Yousuf ya bashi nata ya sashi sanin inda zasu je a yanzu ɗin, dan haka kai tsaye babbar kotun da muke kira da (kotun ALLAH ya isa) dake a jiha ya nufa. Tamkar ba safiya ba harabar court ɗin cike da mutane, hancin motar na kunna kai cikin gate ɗin wasu gungun ƴan jarida suka yomusu caa, isowar securitys da ke son hana ƴan jaridar isowa garesu ya ɗan maido hankalin mutane kan motar suma. Kafin ya gama kashe motar har an buɗe mata. Fuska a yamutse da ɗan jan tsoki ta kalla harabar court ɗin. Wanda ya buɗe matan ta miƙama tarkacen hanunta tare da rigarsu ta lauyoyi. Ita kuma ta ɗauki handbag ɗinta bayan ta toshe fuska da wani shegen gilashi mai tsananin ƙyau ta haɗa da hular, dai-dai tana ficewa ta balla masa harara da faɗin, “Saura nan ma kace zaka biyoni kaga yanda zan baka mamaki”.
Da kallo kawai ya bita, sai kuma ya ɗan furzar da iska ransa fal mamakin yanda bata gajiya da masifa. Da ga can ƙasan ransa kuma yanda ake ta bata wani girma da kariya da ga security ɗin da zallon da ƴan jarida ke faman yi na son isowa gareta ya ƙara ɗaure masa kai da jin takaicin da sun san wacece a zahirinta da ko kallon mutuntawa bata cancanta a garesu ba. Bai iya ɗauke idanunsa garesu ba dan takaici har suka shige wata ƙofa ba ainahin ta Court ɗin ba. A take ya ga gurin ya sake ribcaɓewa, mutane sai faman ɗura kai suke cikin court ɗin. Maganar wasu samari da ke wuce motar cikin ƙaucin shiga kotun ta ɗan ja hankalinsa. Na farko mai riƙe da camara ke faɗin, “Yaufa akwai ƙura, dan na tabbatar barrister Mawaddat Jiƙamshi ba ƙaramin sabon shiri tayo ba duba da yanda Barrister Marafa ya nema zubar da ita a wancan zaman. Kasan fa ita bata taɓa bari a kaita ƙasa musamman a kan irin wannan case ɗin na fyaɗe, ga shi tasan aikinta lawyers ƴan uwanta da yawa har tsoron karawa suke da ita, dan ita ko waye ma ubanka akan fyaɗe sai tayi kutu-kutun turaka jail dan haka kullum ita bata kare mai laifi sai wanda aka zalunta musamman ƴan uwanta mat…….”
Bai ƙarasa jin abinda saurayin ke son faɗa ba dan sun masa nisa. Da farko baiyi niyyar shiga wajen ba, sai dai saboda gargaɗinta ya ƙudiri shigar dan yaga mizata iya masan. Ƙoƙarin fitowa yay a motar kira ya shigo wayarsa. Kamar zai share sai kuma ya cirota da ga aljihu. Ƙanwarsa ce mai bimasa Hawwah dake auren abokinsa. Ɗagawa yay, sai dai yana kaiwa kunnesa yay saurin janye wayar yana mai lumshe idanunsa. Buɗesu yay a hankali zuciyarsa na wani irin zallo. Cikin motar ya koma tare da sake kiranta. Ringing ɗaya ta ɗauka. Cikin matsanancin kuka ta ke faɗin, “Yaya dan ALLAH ka barni na taho gida. Wlhy na gaji da wannan rayuwar bazan iya ba. Inko ba haka ba wataran sai mahaifiyar Abban Nasreen ta kasheni a gidan nan….”
Iska ya ɗan furzar mai ɗaci, tare da faɗin, “Miya kuma faruwa?”. Sake fashe masa tai da kuka, da ƙyar ta iya faɗin, “Mai fa da nake suya airish ma Nasreen da zata wuce school ta kusa kwaramin yau a jiki Yaya. Ban san wane irin rashin ƙauna matar nan take min ba. Wlhy bazata taɓa canja halinta ba nima na gaji da haƙuri da ita.”
“Shi ina Sa’id ɗin yake?”.
“Yaya yana fa a gidan, gashi can ya jata wai yana bata haƙuri saboda ni ba’a san ciwona ba. Yanzu Yaya data sameni da man nan haka zai tsallakeni ya bita ke nan….”
“Kinga ya isa. Ki jirani gani nan zuwa gidan yanzu”. Da ga haka ya yanke wayar batare da ya jira abinda zata ce ba. Fitowa yay a motar ya kulle. Da ƙafa ya fita a habar court ɗin da ta yi tsittt alamar an fara shari’ar ko za’a fara. Yana fitowa a gate ɗin ya samu napep zuwa Daurawa anguwar da gidan ƙanwar tasa take. Kasancewar safiya ce basu wani samu matsala ba, dan haka suka iso da wuri. Bayan ya biya mai napep ɗin maimakon shiga gidan kai tsaye ko yin knocking sai ya ɗaga waya yay kiran abokin nasa Sa’id Ibrahim da sukai karatu a jami’a tare. Yanda Sa’id ɗin ya ɗaga wayar ta isa tabbatar da a rikice yake. Dan duk ya daburce sallamar ma da in ina yayi ta. Sai kuma ya shiga kame-kamen gaisuwa. Katsesa Smart ɗin yay da faɗin, “Gani a ƙofar gidanka ka turo min Hawwah zamu wuce gida”.
“G…g…gida kuma Mawashi? Miya faru ka…k…kake wannan maganar haka? Ko itace ta kira ka ta faɗ……”
“Sa’id!!”.
Ya dakatar da shi a harzuƙe. Sake tsurewa Sa’id ɗin yayi dan yasan halin abokin nasa sarai. Bai da yawan magana ko hayaniya, dan bai taɓa ji ko ganin abokin faɗan Smart Mawashi ba a rayuwa. Amma shi kaifi ɗaya ne akan komai da kowa. Duk yanda yake da kai bai yarda ka latsashi ba ko gasu abokai. Yanda ya rikice ɗin sai ya harzuƙa ran mahaifiyarsa da ta hanashi fita duba matarsa. Dan ta rantse ko bakin ƙofa yaje domin Hawwah ɗin sai ta tsine masa. Cikin masifa ta wafce wayar, kunnenta ta kai da faɗin, “To ɗan mulkin mallaka wai shin nikam ko kai ne ka haifa min Sa’id ne ban sani ba? To bazai zo ɗin ba, nace bazai zo ba idan ka isa kai duk abinda kake jin zaka iyayi, ko ita ƙanwar taka autar mata ce da in ya rabu da ita zai kasa cigaba da rayuwa har ya auro wasu huɗun. Aikin wofi kawai anga kuɗi an nanema yaro na”.
Har tayi ta gama bai ce uffan ba, sai da yaji tayi shiru ya yanke kiran. Yanda yake huci zai baka tabbacin sanin ran ƴan maza ya kai ƙololuwar ɓaci. Number Hawwah yay kira, bugu ɗaya ta ɗaga. Kafin tace komai ya ce, “Ɗakko mayafinki ki sameni waje”. Ya yanke kiran. Minti shida kuwa bata gama cika ba sai ga Hawwah da ƙaton akwati da Nasreen ƴar shekara huɗu biye da ita. Tana ganinsa ta cilla da gudu garesa tana faɗin, “Oyoyo Uncle”. Kaɗan ya saki murmushi, tare da duƙawa ya ɗauketa ita da school bag ɗin da ke goye a bayanta alamar an gama mata shirin makaranta ne. Sau ɗaya ya kalla ƙanwar tasa ya kauda kansa. Batare da yace komai ba ya amshi akwatin hanunta yay gaba tabi bayansa. Napep ya tare musu suka shiga, Nasreen nata zuba masa surutu dan yarinyar ko akku haka ta ganta ta bari kamar ƴar ƙwa-ƙwa akwai wayon jaraba. Dan bakinta ya girmi shekarunta. Sai da ya kaisu har gida sai dai bai shiga ba yace taje ta jirasa zai je ya dawo. Bata musa ba ta fita, shi kuma yace ma mai napep ya juya da shi babban kotun dake jaha. Ya samu har an fito da ga shari’ar, yanda harabar kotun ke’a harmutse da ƙayataccen murmushin da ya hango a fuskar Lulu ya sashi tsira mata idanunsa. Tsaye take a tsakkiyar lauyoyi ƴan uwanta wanda da alama duk ƴan ɓangare ɗaya ne a shari’ar, dan yanda fuskokinsu ke a washe kamar ita saɓanin waɗanda ke gefensu kaɗan zai baka tabbacin hakan. Ƴan jaridar da suka zagayesu ya sashi daina iya hangota, ɗauke kansa yay tare da buɗe motar ya shiga, a kallo ɗaya zaka fahimci damuwar dake zagaye da fuskarsa, dan babu abinda ke faman masa kai kawo sai batun ƙanwarsa Hawwah, shi shaida ne Sa’id na matuƙar son Hawwah, sai dai matsalar mahaifiyarsa da tun farko ta nuna bata son auren saboda ƴar ƙanwarta da taso ya aura shi kuma yaƙi tsayawar mahaifinsa ta sa ta janye ta amince ya auri Hawwah, sai dai tunda take gidan mahaifiyar tasa ke nuna mata hantara da ƙyara musamman idan Alh. Ibrahim mahaifin Sa’id ɗin baya gari. Tasha marin Hawwah ɗin dayi mata abubuwa masu cin zuciya shi yana zuwa ya sasanta bada sanin iyayensu ba. Sai dai a wannan karon ya fahimci dole ne fa a tauna tsakkuwa dan aya taji tsoro. Dan tsohuwar na buƙatar sanin Hawwah nada gatan iyaye da dangi itama, sannan dukiya ba itace rayuwa ba kawai akwai muhimman abubuwa da suka fita a zamantakewar rayuwa. Kai dai kai fatan kawai ALLAH ya rufa maka asiri kafi ƙarfin yau da gobenka. Idan kuma ya azurtaka da dukiyar ka bida ita ta hanyar da kai a karan kanka zakai alfahari da kanka watarana da zaka amsa tambaya akan dukiyar kwabo bayan kwabo……..✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣4️⃣
………Gigitaccen knocking ɗin da akai ma glass ɗin motar ne ya sashi dawowa hayyacinsa. A hankali ya buɗe idanunsa da sukai mugun kaɗawar ɓacin rai ya sauke a kanta. Harara ta balla masa da juyayyun idanun nan nata da shaye-shaye ya gama canjawa yanayin kallo.
“Kai anya kuwa ka taɓa shiga ajin makaranta? Dan na fahimci baka san aikin ka ba, malalacin banza kawai ka zauna kanama mutane tunanin iska a mota, ko an gaya maka a banza ake mallakar irin motar har ai zaman tunani a cikinta Mtsowww!! Baƙauye”. Ta buɗe motar a fusace ta shige tare da rufe murfin da ƙarfi. Fitowar da yay niyyar yi buɗe mata ya fasa, batare da ya tanka mata ba kamar yanda ya saba yayma motar key. Bata sake bi takansa ba ta maida hankalinta a lap-top itama, yayinda shi kuma yake tafiya a nutsensa. Sunyi nisa sosai batare da ko sau ɗaya ta ɗago taga ina suke nufa ba, dan ita duk zatonta hanyar office ɗinta ya nufa da ita tunda Uncle Yousuf yace mata ya bashi komai nata a rubuce. Jinfa tafiya na neman ƙin ƙarewa ya sata ɗagowa. Da sauri ta ƙara ware Lulu ayes ɗinta tana kallon inda zata iya rantsewa bata taɓa sani ba ma, dan ita dai kusan yawonta wajen Kano a jirgi ne. Gabanta ne ya faɗi, zuciyarta ta shiga mata kai-kawon ko yayi kidnapping ɗinta ne? Amma sai ta dake a masife ta ce, “Kai malam mi kake ƙullawa ne? ina ne kake shirin kaini nan?”.
Shiru kamar bazai tanka mata ba, dan har ya kunnata ta ƙara ƙarfin hucinta. Sai kuma cike da rainin wayo ya bata amsa cikin halin ko’in kula da cewa “Asibiti ganin likitan ƙwaƙwalwa”. dai-dai yana ƙoƙarin shiga ƙaton gate ɗin asibitin na dawanau.
“What?! Wai nice ka kawo duba masu taɓin ƙwaƙwalwa kake nufi ko mi?”. Tana sake ware idanunta kan rubutun saman ƙaton ginin inda yay parking. Bai tanka mata ba har sai da ya kammala dai-daita motar a gaban wajen. Kasheta yay gaba ɗaya tare da kai idanunsa kanta ta cikin mirror. Kallon nasa kuwa take itama dan tsabar takaici ya hanata iya sake cemasa komai amsar dalilin zuwansu kawai take buƙata da ga garesa.
“Kinada kati anan ne ko yau za’a fara yankar miki? Dan naga kamar ƙwayar da kika sha jiyan bata kammala sakinki ba”. Ya faɗa a dakensa.
“Kai! Wai dama ni kake nufin inada taɓin ƙwaƙwalwar ma kenan?”.
Idanunsa da take kira na macizai ya wara mata cike da salon sake tura mata takaici. Sai kawai taji ƙwalla na neman cika mata idanu. Tunda take a duniya bata ko tuna an taɓa wulaƙantata makamancin yau ba, ba zuciyarta ba hatta numfashinta fita yake da sassarfa. Wai ita wannan ya kawo asibiti, asibitin ma na masu taɓin hankali. Babu abinda take ji a ranta kamar ta haɗama ƙyaƙyƙyawar fuskarsa jini da majina da maruka fiye da yanda ya yagata, ta dunƙule hannunta amma hannun ya gagara ɗaguwar aikatawa. Maimakon ma hakan kanta kawai ta dafe dan jin zuciyarta na barazanar tsagewa biyu. Batajin idan ta sake kai mintina sama da uku a motar nan bata shaƙe mutumin nan ya bar duniya ba. A wani irin harzuƙe ta bankaɗe murfin motar ta fita, inda yake zaune mazaunin driver ta buɗe. Shi kansa bai taɓa ganin ɓacin rai tattare da ita irin yau ba, dan tsabar masifa fuskarta har jaja takeyi….
“Fitar min a mota!!”.
Ta faɗa da ƙyar muryarta har rawa takeyi. Cikin deep voice ɗin nan tasa da sake dakewa ya ce, “Maizasa na fita bayan akan aikina nak…..”
“Wlhy zan kashe fuskarka da mari idan baka fitar min a mota ba tunda ban haɗa kuɗi da kai na saya ba!!”. Ta sake faɗa a wani yanayin da muryarta ke fita da cracking. Ya gama sanin ta kai ƙololuwar fusatar da yake buƙata, dan haka cikin taɓe baki ya fice yana wani murmushin da ke sake tafasa mata ruhinta shiko yana sake ƙayatar da kwarjininsa.
“Ka rubuta ka ajiye sai na wulaƙanta rayuwarka a mizanin mafi munin wulaƙanci”. Ta faɗa dai-dai tana fisgar murfin motar bammm! Ta rufe. Kamar yanda ta saba a guje ta fice a asibitin, dan Lulu akwai iya tuƙin ganganci da wauta balle yau da ya zama an kunnata ne, shiyyasa Daddy yafi son driver ya jata a mota. Da gaske tuƙi take irin na wauta da isa, har takai wasu drivers ɗin na zaginta idan tai wani abun cike da gadara. Tana kan round about ɗin da zata ɗauki titin office ɗinsu ta kusa haɗa accident sakamakon neman shallakewar ƙin tsayama traffic light data nema yi. A fusace drivern data dakarma mota ya fito, itako babu alamar ko ɗar a tare da ita ta ƙara sautin kiɗan wakar Shakira da ke tashi a motar, dan tana matuƙar son waƙoƙin mawakiyar, shiyyasa bata da wakar data bama amanna kamar waƙoƙinta musamman idan tana cikin ɓacin rai irin haka.
“Ke ƴar uban wacece da zaki da kar min mota ki cigaba da zama a ciki kamar bakiyi ko mai b……..” ya gagara ƙarasawa saboda tozali da abinda baiyi zato ko tsammanin gani ba. “Ni ƴar gidan ubanka ce!!”. Lulu da dama take a harzuƙe jira take a taɓata ta fashe ta bashi amsa a fusace itama. Kansa ya ɗan dafe da wani irin salo yana juya jikinsa kaɗan, sai kuma ya sake jiyowa gareta da ɗan kuzari ya ranƙwafo a motar. “Oh Baby dama ke ce? Please am so sorry”.
Harara ta balla masa tare da jan sirrin tsaki ta ɗauke kanta. Zai sake magana ta ɗaga masa hannu, tare da ɗakko bandir na sabbin dubu ta jefa masa a harzuƙe. “Ko basu kake buƙata ba dama?”. Siririyar dariya ya saki mai ƙayatarwa. “Mai sunan gwaggo kenan, ni bance ina buƙata ba, sai dai idan kin bani ƙyauta ne zanso haka. Koba komai ƙyauta da ga masoyiya zuwa masoyi ai abin alfahari ne ko”.
“Tajuddeen bani hanya na wuce kafin kaja na sauke maka abinda ke kaina wlhy!! Dan inada abunyi”.
“Zan iya ɗaukar ko miye da ga kanki ko mi nauyinsa, sannan nima inada abunyi dan haka ma kika ganni da farar safiyar nan akan titi, duk da dai naci ribar fitar kodan ganinki da nayi”.
Maimakon amsa masa sai taja tsaki, tare da yin sama da glass ɗin motar. Da sauri yaja da baya dan neman takashi take yi. Cikin murmushi da cizar lips ya duƙa ya ɗauki kuɗin nan data jefesa da su a ƙasa yana kaisu hancinsa dan tuni ƙamshin turarenta mai ƙarfi ya mamaye su. Duk abinda ke faruwa akan idanun Smart ne da ke cikin napep kamar sauran mutane, dan tana baro asibitin yay murmushi, sai dai da sauri shima ya fito saboda ganin yanda ta fisgi motar cike da ganganci ya kuma san bata san hanya ba sosai, baya fata wani abu ya sameta a dalilinsa, cikin sa’a ya samu napep, dan haka yace masa su bita, sai dai tuni ta musu fintinkau saboda gudun da take zubawa dan har ta ɓace musu, sai gashi kuma sun haɗu a traffic light ɗin. Ƴar hayaniyace ta fara tashi, wasu na zagin Lulu wasu najin haushin Tajuddeen da ya taso gigigi ya kuma koma yay sakwat, daka gansa dai shima kasan akwai nerar balle ace saboda kuɗin data watso masa ne. Sai dai wasu sun fahimci ma dai kamar sun san juna ne shiyyasa, amma hakan bai hana ƙananun maganganun ba dai. Sirrin tsakin da bai shirya bane ya fita a bakinsa a karo na farko. Yana ƙoƙarin ɗauke kansa da yima mai napep maganar su juya titin anguwarsu dan ya fasa bin bayanta da yay niyya idon Tajuddeen ya sauka a kansa. Murmushi ya sakar masa da ɗaga masa hannu, hakan yasa shi dole fitowa fuskarsa a ɗan sake shima ya miƙa masa hannu suka gaisa. “Ya naga yau tafiyar taku daban-daban? Koda yake da alama yau ogar taka fitina take ji”. Tajuddeen ya faɗa da alamar ƴar damuwa, dan harga ALLAH yana matuƙar son Lulu. A karo na farko Smart ya ɗan saki murmushi mai sanyi. Cikin nutsuwar nan tasa, sai dai a can ƙasan maƙoshi ya furta “Ita dama kullum a cikin rigimar take ai. Tunda ta tsere mana ma zan juya gida ne kawai”.
“A’a ba’ayi haka ba. Bari mu ƙarasa dan office ɗin nasu kusa yake damu”. Badan Smart yaso ba Tajuddeen ya biya mai napep da ya ɗakkosa, shi kuma suka shiga motarsa a tare. Tunda suka bar wajen Tajuddeen ɗin ke jansa da hira. Shi dai nashi murmushi ne kawai bai iya cewa komai. Tajuddeen ya fahimci Smart bamai yawan magana bane, sai dai sam baza’a taɓa kiransa miskili ba. Kawai dai shiru-shiru ne shi bai cika hayaniya bane. Tafiya kaɗan ta kawosu, guri ne mai ƙyawun gaske da ɗan girma dan gaskiya ya tsaru. Tajuddeen yaso su shiga tare da Smart amma yaƙi ya ce ya barsa anan wajen, badan yaso hakan ba ya barsa nan jikin motar shi kuma ya shige. Ya ɗan gaisa da tsirarun ma’aikatan da suke kai kawo saboda sun sanshi dan lokaci zuwa lokaci yakan ɗan zo wajen Lulun, da ga haka ya nufi lifter zuwa 3floor. Offices ne kusan goma a wajen, a office na kusan bakwai, a hankali idanusa suka sauka kan rubutun saman da aka rubuta. *_Barrister Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi_*.
Kai tsaye Tajuddeen ya shige babu wani neman excuse, ƙaramin falo ne dan table ɗin sakatariyarta ne kawai sai kujeru uku 3sitter da 1sitters guda biyu da table a tsakkiyarsu. Da ga ɗan gefe kaɗan water dispenser ce mai ƙyau sai tv da ke maƙale acan sama. Glass ne ya raba wajen da office ɗin ta, dan haka ya iya hango yanda take ma wata dake tsaye gaban table ɗin ta masifa, duk da bajin mi take faɗa yake ba yanayin yanda take karkaɗa hannu ya bashi tabbacin hakan. Da sauri Tajuddeen ya tura ƙofar ya shiga, a tare Lulu da sakatariyarta da ke shan masifa dan a kanta ta hau juye takaicin Smart suka juyo……..✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣5️⃣
……..Fuska Lulun ta sake tsukewa, yayinda sakatariyar ta risina tana gaishesa dan tasan ko wanene tunda ba yau ya fara zuwa ba.
“Jeki abunki”.
Ya cema sakatiyar yana kaiwa zaune. Sakatariyar ta ɗan kalli Lulu a tsorace, sai kuma ta dubesa cikin girgiza kai kamar zatai kuka. Shima Lulun da ke faman haɗa takardun gabanta ya kalla, sai kuma yay ɗan murmushi. “Madam please taje?”. Harara ta ɗago ta balla masa, ta sake maida kanta ga abinda take yi. Ƴar ƙaramar dariya ya ƙarayi mai fidda haƙora, tare da yima sakatariyar nuni da hannu alamar taje. Da sauri ta fice har tana neman cin tuntuɓe. Idanunsa da ke ma sakatariyar kallon ƙasa-ƙasa ya janye ya maida ga Lulu… “Miyasa ka biyoni?”. Ta katse maganar da yay yinƙurin mata. “Idan masoyi ya biyo masoyiyarsa laifi ne Mawaddat. Please ki daina wahal damu haka mana, ko so kike sai na kai ƙasa ne?”.
“Bani da matsala da kaiwarka ƙasa Tajuddeen, matsalata ɗaya shigarmin rayuwa da kake yi. Ka bar wahal da kanka dan bazaka taɓa samuna ba. Ko’a baya na amince ma batun su Daddy ne saboda Grandpa kaima ka sani. Amma ban taɓa jin sonka ba, kai bama kai ba, duk wani namiji ban taɓa jin sonshi da sunan soyayya ba a rayuwata. Idan ka cire Daddy na, Grandpa, da Uncle you. Ina baka shawarar ka daina bibiyata dan ina ɗaga maka ƙafa ne saboda zumincin da ke tsakaninmu, idan kuma ka cigaba zan iya fyatoka ta duk inda yay mun bawai hancina kawai ba”. Daga haka ta miƙe hannunta ɗauke da takardun data tattara. Cikin takun nan nata na yauƙi. Tamkar wanda ta danne bakinsa da dannau ya kasa iya furta komai sai binta da kallo da yay cikin tashin hankalin kalamanta. Ya jima da fahimtar bata ra’ayinsa a yanzu, amma bai taɓa tunanin tun farko ma bata taɓa sonshi ba alfarmar Grandpa ɗin su yaci ba. Hannunsa ya kai saman goshinsa ya shiga murzawa, dai-dai nan sakatariyar Lulu ta shigo. Ɗagowa yay yana kallonta, ta ɗan rissina da girmamawa ta ce, “Sorry sir ta ce na rufe mata office ɗin”.
Idanu ya ɗan lumshe ya sake buɗewa akan matashiyar yarinyar mai tarin nutsuwa. Sai kuma ya saki murmushi da jinjina mata kansa ya miƙe kawai. “Sorry sir” ta sake faɗa dai-dai yana fita. Hannu kawai ya ɗaga mata batare da ya juyo ba ya fice abinsa zuciyarsa fal damuwa. Koda ya fito ƙurar motarta kawai ya samu alamar ta fice. Ya kalla Smart da ke jigine jikin motarsa da waya a kunne alamar magana yake. Tsaiwar jiransa yay har ya kammala. Bayan ya kammala wayar ya juyo idonsa akan Tajuddeen da fuskarsa ta nuna alamun ɓacin rai da damuwa, kai tsaye ya furta, “Inaga zan wuce gida dan wani uziri ya taso min”. Cikin damuwar dake shimfiɗe a fuskarsa ya gyaɗa masa kai da ɗan ɗage kafaɗa. “Ba damuwa ai itama ta sake tafiyarta”. Sam shi Smart bai ga fitar Lulu ba, dan haka ya kallesa cikin son ƙarin bayani. “Ina magana ne akan ogarka bakaga fitar ta ba?”. Smart ya kai dubansa ga inda ya ga motarta tun shigowarsu, wayam babu ita. Sai kawai ya dawo da dubansa akan Tajuddeen ɗin yana mai girgiza kansa da ɗan furzar ya huci. A taƙaice ya ce, “Bara na wuce”. Ba yanda Tajuddeen ɗin baiyi ba akan ya bari ya kaisa amma yaƙi. Dole sukai sallama ya fito domin samun napep…..
★★★
Sosai ran Tajuddeen yake a dagule, dan haka maimakon office da yay niyyar zuwa sai ya nufi companyn mahaifinsa da yake da tabbacin yana can. Koda ya isa gaisuwar ma’aikatan wajen ma bai iya amsawa da ƙyau, hannu kawai yake iya ɗaga musu. Sun sha mamaki dan sun san shi mutum ne mai saukin kai sosai ga fara’a. Sam baida wulaƙanci, wani lokacin ma idan yana jin barkwancinsa ya shigo Companyn bazaka taɓa cewa ɗan oga bane ba. Kai tsaye office ɗin mahaifin nasa ya nufa batare da jiran sakataransa yay masa iso ba. Alhaji Sulaiman Sufi Garko da ke tsaka da tattaunawa da babban yaronsa da ba’a jin sirrinsu a tare suka zuba ma Tajuddeen ɗin ido har ya ƙaraso inda suke. Hannu ya Bama yaron mahaifin nasa mai suna Isyaku, sai dai ana kiransa da Malami. Malami ya gaida Tajuddeen ɗin da girmamawa duk da kuwa zasu iya sa’anni, to amma ai baba ma da babansa. Alhaji Sulaiman dai kallon ɗan nasa yake kawai bai dai tanka ba, sai wani inkiya da yayma Malami da ido. Kai ya gyaɗa masa dan babu wani yaren jiki na Alhaji da bai haddace ba. Ko tari yayi yasan mi yake nufi. Fita yay ya bama ɗa da mahaifin waje…
“Auta wani abu ya faru ne na ganka a haka?”.
Alhaji Sulaiman ya faɗa cike da kulawa ga tilon ɗan nasa namiji kuma auta a cikin ƴaƴansa. Cike da damuwa Tajuddeen ya sake tsuke fuska, sai kuma ya kalla mahaifin na sa da idanunsa da suka kaɗa sosai. “Abba Please ina son zancen aure na da Mawaddat ya motsa mana. Wlhy bazan iya daina sonta ba, dan na gwada hakan amma na kasa”.
Murmushin manya Alhaji Sulaiman yayi tare da ajiye pen ɗin hannunsa idonsa ƙyar akan Tajuddeen kamar yana son tabbatar da gaskiyar furucinsa…
“Abba Please say something mana”. Tajuddeen ya faɗa kamar zai saki kuka.
Alhaji Sulaiman ya furzar da huci yana mai haɗiye sauran murmushin fuskar tasa da ya rage. “Tajjudeen in ce maganar nan ta wuce ai ko?”.
“Abba bata wuce ba wlhy, dan nikam ina sonta kuma zan zauna da ita a duk yanda take. Dan ALLAH kayi haƙuri ku sasanta da Uncle Isma’il ni dai a auramin ita. Kaga zuwa jibi Grandpa zai dawo da ga Umra ɗinsa, ni dai zan samesa da zancen a karo na biyu tunda har yanzu bawai ta tsaida wani mijin bane. Nima kuma na kasa kallon kowacce mace da sunan soyayya dan ita kaɗai nake so tun ina yarona”.
“Humm Tajuddeen sasantawa tsakanina da Isma’il abune mai matuƙar wahala. Kuma nasan zai iya wulaƙantani fiye da da saboda ƴarsa. Amma zan iya komai a kanka kamar yanda shima yake jin zai iya komai akan tasa ƴar. kuma kafin ma Baba ya dawo jibin yau zan fara masa zancen a waya”.
Sosai farin ciki ya baibaye zuciyar Tajuddeen. Miƙewa yay yaje ya rungume mahaifin nasa. Shima fuskarsa da murmushi ya amshesa hannu biyu. Kusan mintuna biyu Tajuddeen ya ɗago. Cikin komawa serious ya ce, “Abba wai dan ALLAH miye ya haɗaku kai da Uncle Isma’il? Nasan dai sanda ina yaro ba haka kuke ba. Kuna ƙaunar juna kamar ƴan uwa na jini, kuna mutunta juna matsayin surukai. Amma abin mamaki sai ga mijin ƙanwarka uwa ɗaya uba ɗaya ya juye ya zama maƙiyika! Abba Please ka sanar min miya haɗaku ko zan iya wani abu mana”.
“Tajuddeen wannan ba huruminka bane, kai dai ba kana son auren Mawaddat bane? To ka saka a ranka kamar ka samu dan koba komai ita ɗin ɗiyar ƙanwata ce Isma’il bai isa canja wannan tarihin ba. Dan haka jeka ka cigaba da harkokinka Mawaddat ta zama matarka nan da sati biyu kacal”.
Sosai maganar farko ta tsaya masa a rai, sai dai ta ƙarshe ta masa matuƙar daɗi da sakashi a farin ciki dan haka bai musa ba yay masa sallama ya fita cike da ƙwarin gwiwar ya kusa mallakar Mawaddat.
Ni dai nace hummmm😵💫. Kufa masu karatu ya kuka gani🤷?.
★★★….★★★
Kallon mamaki yake ma matar tasa akan furucinta. Fahimtar hakan ya saka Aunty Saliha sake faɗin, “Wlhy da gaske nake Sweetheart bata nan fa. Alamu ma ya nuna ta jima da barin gidan nan kamar”. Sosai ran Uncle Yousuf ya sake dugunzuma. Dan haka ya cije lips ɗinsa da ƙarfi batare da yace komai ba. Ture shayin gabansa yay tare da miƙewa ya fice a falon. Cike da tausayin mijin nata ta bisa da kallo. Baba maigadi ya gaishesa da girmamawa duk da ganin yau fuskar ubangidan nasa babu walwala. Hannu kawai ya iya ɗaga masa. Sai kuma ya furta “Baba ko akwai wanda ya fita a gidan nan ne bayan yara da suka wuce school?”.
Baba maigadi da ya ɗan daburce ya shiga in-ina da inda-inda. “Baba tambayarkafa nake? Bana son kwane-kwane ka faɗa min”. Uncle Yousuf ya faɗa da ɗan jin haushi a muryarsa. “Kayi haƙuri Alhaji, abunne dai kamar da ruɗewar kai. Hajiya Muwaddat dai ta fita kam tunda duku-duku kafimma yara su wuce, sai dai abinda ya ɗauremun kai da hargitsani ni banga shigowarta bane shiyyasa na fara tunanin ko junnu ne ke son buɗe min idanu n….”
Takaici ya saka Uncle Yousuf yin gaba batare da tsayawa jin ƙarashen labarin da yayma kallon na soki burutsu ba. Sai dai harga ALLAH shi baba maigadi iya gaskiyarsa da yake faɗa. Sosai hankalin Uncle Yousuf ɗin ke’a tashe, dan zuciyarsa ta fara masa wasi-wasin karfa taƙi zuwa gida. Yana shiga key ɗin motarsa da ke a dining kawai ya bama aunty Saliha umarnin bashi, bai ma ko saurareta akan magiyar yazo ya ƙarasa break fast ɗinsa baiyi ba ya sake ficewa abinsa. Sai ƙarar buɗe gate da fitar motarsa kawai tajiyo. Addu’ar isa lafiya kawai tai masa dan bata da yanda ta iya tunda tasan ƙaunar da yakema ahalinsa dabance a rayuwa. Bai haɗa son su da komai ba. Ita hakan bai taɓa zame mata matsala ba dan itama suna nuna mata ƙauna a cikinsu. Basu taɓa wareta ba ko nuna mata bambancin kasancewarta bare garesu. Hasalima suna ɗaukar mahaifinta matsayin uba garesu a yanzu fiye da kowa har danginsu na Jiƙamshi. Dan haka bazataima ALLAH butulci ba sai dai ma ta tayashi son danginsa itama tare da musu fatan alkairi musamman akan Mawaddat data zame musu tamkar zakka………✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣6️⃣
……..Cikin ƙanƙanin lokaci Uncle Yousuf ya isa gidan ɗan uwan nasa. Anan ma sama-sama ya gaisa da su maigadi. Su ya farama tambayar Lulu tazo gida. Sun bashi amsar da ta sakashi sakin ajiyar zuciya mai kauri. Sai kuma ya samu ƙwarin gwiwar ƙarasawa ciki duk da sun tabbatar masa ta fita aiki tunma ɗazu tare da drivern ta. Kusan karo suka ci da Daddy dake ƙoƙarin fitowa har lokacin yana ƙananun magana wa Mommy akan Mubeen bai gaida Lulu ba. Sai dai duk wanda ya sanshi yaga yanda yake faɗan yasan yana yinsa ne kawai amma akwai abinda ke damunsa mai raɗadi ba abinda Mubeen ɗin yayi bane, shi kamar ya taka sahun ɓarawo ne. Ita dai Mommy bata tanka ba sai ma maida hankalinta tai akan cin abincinta da shi Daddy ɗin ya fasa ci saboda Lulu bataci ba. Mubeen ma na zaune cikin ɓacin ran yanda faɗansa ya koma kan Mommy kamar dai dama Daddyn nasu dama da biyu ya ƙirƙiri faɗan dan ya maidasa kanta ne. Gaishesa Uncle Yousuf ɗin yayi, sai kuma ya leƙa ya gaida Mommy da ga inda yake tsaye, acewarsa yana sauri ne dama ya biyo ne yaga Yaya. Mommy tai ɗan murmushi da masa addu’a. Tare suka fito da Daddyn da ya bar faɗan tun ganin Uncle Yousuf, dan yasan yana ji zai fara kare Mommy koma shi ya maida faɗan a kansa.
“Yaya magana ce da ni mai muhimmanci”. Ya faɗa cikin rashin walwala. Tsai daddy yay yana kallonsa. Sai kuma ya kamo hanunsa da faɗin, “To muje office ɗina ko naka sai muyi a can ko auta”.
“A’a Yaya, anan gida ya cancanta muyita dan zatafi dacewa”.
Komai Daddy bai sake cewa ba sai hannun ƙanin nasa da ya sake ja suka nufi falon baƙi da ke can ta wajen garden. Tsaf falon yake dan kullum sai an gyarashi da saka masa turaren wuta. Bayan sun zauna cikin kulawa da san danne damuwa Daddy ya ce, “Ina jinka mike faruwa Auta? Danni duk ka ɗaga min hankali da wannan yanayin naka wlhy.”
Numfashi mai ɗaci Uncle Yousuf yaja da gyara zamansa. Kai tsaye ya ce, “Akan Mawaddat ne.”
“Kuma dai Yousuf? To mi ta sake yi?”. Da ga jin a yanda Daddy yay tambayar kasan ransa a jagule yake. Amma sai Uncle Yousuf ɗin yay biris ya cigaba da faɗin, “Gaskiyar da muke buƙatar gani da ido ce na gani jiya a zahirance. Dan an maido min Mawaddat gida a buge tana warin kayan maye kamar ma harda giya”.
Tsurru Daddy yay yana kallon Uncle Yousuf, sai kuma cikin rawar murya kamar mai shirin yin kuka ya ce, “Yousuf dan ALLAH ka gayamin gaskiya, dan in har wani yazo ya faɗa maka nasan za’a iyama Mawaddat sharri kasanta da magauta. Na rasa mi yarinyar nan ta tsarema wani a rayuwa. Gashi ita bata damu da kowa ba amma ita an dam……..”
Dakatar da shi Uncle Yousuf yay da faɗin, “Yaya! Kasan dai bazan ma Mawaddat ƙarya ba dan naci riba ko? Kuma ni babu wanda yazo ya faɗa min ni na gani da idanuna. Kuma gashi misawarka tasa na fahimci kai kanka baka san Mawaddat bata kwana gida ba ma. Hakan na nufin dama ba yau ta fara fitar dare ba batare da ka sani ba kuma baka taɓa maida hankali ko damuwa ba akan tabbatar da kowa na gida kafin ka kwanta. Yaya bansan yashe ka koma haka ba, shin dan ALLAH miya canjaka? Anya kuwa son Mawaddat kakeyi da gaske har cikin ranka? Wace irin bahaguwar rayuwace wannan mara fasali. Iyayenmu sun baku tarbiyya gwargwadon iyawarsu kai da Aunty Kareema. Sannan kuma kun bani dan gashi a yanzu ina cin ribarta matsayin nagartaccen mutum da ke banbance fari da baƙi koda a cikin rufewar idanu ne. Sannan sauran yaran ma suna samun irin tarbiyyar dana samu da ga gareku. Shin miyasa komai ya canja akan Mawaddat ne? Miyasa makahon so ya lulluɓe zuciyarka kake ɗorata akan abinda zata iya kaico da kai wataran da tunanin soyayya ce. Ban ce karka sota ba, amma ka dinga dubayya mana. Shin dole ne sai ka nuna mata ƙazamar soyayya zamu san kaso mahaifiyarta kamar haka itama? Ko sai ka mata makahon so zai sanarma duniya ita ɗin ƴar sonka ce da ta fito da ga jikin matar son ka?. Anya yaya ba alhakin Aunty Kareema bane kuwa ke bibiyarku akan Mawaddat kai da mahaifiyarta? Anya ba farkawa ya kamata kayi da ga nannauyan barcinka ba a wannan gaɓar kafin komai ya ƙarasa taɓarɓarewa mu rasa Mawaddat gaba ɗayanta”.
Sosai jikin Daddy ya ƙara yin sanyi, dan dama harga ALLAH ƙarfin hali kawai yake na son musawa uncle Yousuf ɗin tunda shima ya ga shigowarta gidan a ɗazun da safen batare da ita ko wani ya sani ba. Wannan damuwar ce ya tashi da ita, sai dai ya rasa ta yanda zai tunkari Mawaddat ɗin shine ya huce haushin akan Mubeen da Mommy. A hankali ya damƙo hanun Uncle Yousuf cikin nasa ya ƙanƙame da ƙarfi, so yake ko sau ɗaya yayi kuka akan wannan damuwar ta halin rayuwar da Mawaddat ta jefa kanta a ciki amma ya kasa. Sai dai idanunsa sunyi wani masifar kaɗawa da ja. Cikin rawar murya ya ce, “Nagode ɗan uwana. Nagode da ka kasance mai faɗa min gaskiya komai ɗacinta. Wlhy auta al’amarin Mawaddat shine mafi zama ƙololiwar damuwata a yanzu fiye da komai, dan hanani barci yake yi. Zan faɗa maka gaskiya ko jiya nasan fitar ta a gidan nan, kuma nabi bayanta, sai kuma na samu yaron nan driver da ka kawo shima ɗin yabi bayanta. Dan haka na laɓe a kangwon kusa da gidan data shiga a wajen har kunama ta harbeni jiyan. Ban damu da azabar kunamarba, ni dai burina yaron nan ya fito da ita a gidan lafiya. Cikin amincin UBANGIJI kuwa sai gashi ya fito da ita a mota, na fito zan sake biyosu duk da azabar harbin kunamar da nake ciki idona ya ganemin ɗan gidan tsohon gwamna M Atik Kumo zai shiga gidan shima. Na shiga tashin hankali matuƙa, sai dai ban tsayaba na biyo motar tata dan naga ina yaron nan zai kawota sai naga gidanka ya nufa da ita. Nutsuwar hakan dana samu ce ta sani komawa da baya can gidan ɗin dai na sake tsayawa a mota, abinda ya sake tadamin hankali Yousuf su Alhaji Baita na gani sun fito a gidan nan dai da Mawaddat ta shiga kusan ƙarfe ukun dare. Wlhy tsabar ruɗani bamma san kunamata ta sauka ba. Da ƙyar na iya sake maido kaina gida shine fa ko rintsawa banyi ba har akai sallar asuba, bayan na dawo massalaci naga shigowarta gidan nan”. Ya ƙare maganar hawayen da yaketa son su zubo na sauka a yanzu masu zafi. Sosai shima Uncle Yousuf ya shiga ruɗani da tashin hankali. Dan jin sunayen manyan mutane da duk wanda ka tambaya zai tabbatar maka ɗunbin ganin mutuncinsu da yake a cikin wannan labari na yayansa……
Daddy ne ya katsesa da faɗin, “Yousuf kaina ya kulle gaba ɗaya akan al’amurin nan, ka kawo mafita inba hakaba ina gab da kaiwa ƙasa akan lamarin Mawaddat”.
“Yaya mafita ɗaya muke da ita shine yi mata aure….”
“Aure Yousuf? To da wa? Kasan dai Mawaddat bata kula kowa. Kana dai ganin duk kurari da jan idon Baba (Alhaji Sufi Garko) yayi ya barta akan sanya ranarta da yaron Sulaiman data bijirewa. Har gargaɗin duk randa wani ya sake zuwa garesa domin santa zai aura masa ita koba amincewar ta da mu kammu yay mata amma bata ɗauki hakan da muhimmanci ba saboda bushewar zuciya. Yousuf na rasa da ga ina na kuskure akan Mawaddat. Shin nuna mata soyayya na nufin ba dai-dai ba kenan?”.
“Humm Yaya wannan harda laifinka kaima ka sani, ba’a hana iyaye su nunama ƴaƴansu soyayya ba, sai dai ba ƙazamar soyayya irin wadda kaima Mawaddat ba da har tazama jagoran hanata fahimtar minene addininta. Yaya kofa salla nagartacciya Mawaddat bata iya ba a wannan shekarun nata balle azo ga sauran al’amuran addini, hakan kuma duk kuskurenka ne da kasa barinta ta samu tarbiyya irinta uwa a wajen Aunty Kareema saboda son zuciyarka….. Amma dai mu ajiye abinda ya wuce mu kalla na yanzu. Yanzu dai bayan tabbatar da aure ne mafitarmu akan lamarin Mawaddat bani da wani idea kuma. Amma dai ka bani lokaci nayi nazari tukunna. Sannan dan ALLAH ka kwantar da hankalinka. Dan lamarin Mawaddat an baro shiri ne tun rani. Amma insha ALLAHU tsayayyen miji a gareta zai jagoranceta da sabuwar tarbiyyarsa irin wadda tun farko ya kamata ace ta samu da ga garemu. Addu’a ya kamata mu duƙufa mata musamman ma kai ɗin nan. Sannan mu dage da sadaka ALLAH ya shiryar mana da ita, ya kuma kawo mana mafita cikin sauƙi. Sannan ka ajiye batun su Alh. Baita ni da kaina zanyi bincike a kansu insha ALLAHU zan gano alaƙarta da su”.
“Shike nan Yousuf ALLAH yay maka albarka.”
“Amin yaya”.
Daddy ya sake nisawa a hankali da faɗin, “Sai dai kabi a hankali a duk wani bincikenka dan a wannan gaɓar da gaske inajin ƙanina, tsoro na gaske nakeji wlhy a wannan gaɓar. Miya kawo su Alh. Baita cikin rayuwar Mawaddat?”.
“Bana tunanin wani abu saɓanin wanda zuciyata ke kallo yaya. Kasan dai da yawan wasu manyan ƙasar nan sunata taka wata rawa cikin rayuwar lalacewar yaranmu batare da mun farga ba”.
“Nafika sanin hakan Yousuf. Sai dai al’amarin ya wuce a yanda kai kake kallonsa da hasashensa. Kai dai kamar yanda na faɗa maka inajin tsoro da gaske a yanzu tsoro nake ji irin wanda a baya babu shi a zuciyata…..”
“Yaya na kasa fahimtar mi kake nufi ka ruɗar dani fa, Miye ke baka tsiro ne wai?”.
Murmushi Daddy yayi mai nuna tsantsar damuwa a bayyane. Maimakon amsa sai ya dafa kafaɗar Uncle Yousuf tare da ɗan bubbugawa ya miƙe. “Tashi kaje office auta karka makara”.
Kallo Uncle Yousuf ya bisa da shi mai tsayawa a rai, sai zuciyarsa ke wani irin rawa dan shi kaɗai yasan mi yake iya hangowa game da ɗan uwan nasa, sai kawai shima yaji kamar ya fara jin tsoron. Tabbas akwai ɓoyayyen al’amari wanda ya kamata ace ya sani amma ta yaya? (Bincike akan alaƙar Mawaddat da su Hon. Babale Nakowa) kansa ya jinjina cikin gamsuwa da shawarar zuciyarsa. Dan haka shima ya miƙa ya fice. Da kallo yabi motar Yayansa dake ƙoƙarin ficewa a gidan. Numfashi ya sauke da ƙyar tare da nufar tashi motar shima.
★★★ ∆ ★★★
Smart kam tattara al’amarin Lulu yay ya wancalakar gefe domin fuskantar tasa mai muhimmanci. Gida ya nufa kai tsaye saboda kiran da Abba yay masa. Ya samu gidan da ƴar hayaniyar kasancewar zuwan Sa’id da wasu kawunansa uku. Cikin girmamawa ya gaishesu batare da ya kalla inda Sa’id ya ke gurfane ba kamar mai kuka. Ya maida hankalinsa ga Abba da Hawwah ke a kusa da ƙafafunsa kamar tana kuka itama.
“Abba gani”.
Ya faɗa cikin dakewarsa. Nisawa Abba yay da nuna Hawwah ya ce, “Kaine ka ɗakko Hauwa’u a gidanta?”.
“Eh tabbas nine Abba”.
“Me yasa?”.
Shiru ya ɗan yi kafin ya nisa. “Abba saboda ta kirani akan ga mahaifiyar mijinta na neman ƙonata da mangyaɗa. Banje gidan da nufin ɗakkota ba sai jin ba’asi na kuma sasanta kamar na baya da akai batare da kun sani ba. Sai dai na samu abin ya wuce yanda nake zatonsa shiyyasa na ɗakkota kafin a cutar da ita tunda mu bawai mun daina sonta bane ba. Ba kuma mun bashi bane dan mun gaji da ita a gidan nan kota gundiremu. Abba abubuwa da yawa sun faru akan auren Hawwah amma ina sasantawa a iya can batare da kai ko Ammah kun taɓa sani ba. Bama ku ba hatta da Aunty Bilkisu ban taɓa sanarmawa ba, kuma na gargaɗi Hawwah sanar ma kowa. Shiyyasa wannan karon na ɗakkota kuma bazata sake koma musu gida ba. Yaje ya auri wadda mahaifiyarsa ke son zama da ita haka nan dan ALLAH kowa ya huta.”……..✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣7️⃣
……..Cikin ɓacin rai ƙanin mahaifin Sa’id ya ce, “Ai ba ita kaɗai ce keda iko da shi ba. Sannan kuma ni banga laifinka anan ba yaro. Hasalima abinda kai sai ka birgeni dan kayi abinda ya kamata ace ƴan uwa na ƙwarai suyi akan ƙannensu. Wannan shine girman kuma shine darajtawar.”
“Tabbas abinda yay yayi dai-dai. Kuma tunda hakane muma kan zamu fidda kammu a wannan zancen ku ɗauki duk matakin da kuke gani shine dai-dai dan halin Rafi’a sam bashi da burgewa. Narasa mitake son maida kanta a rayuwa ita ba ƙaramar yarinya ba amma kullum aita abu guda kamar cin ƙwan makauniya, yanzu da tsautsayi yasa ta samu yarinyar nan da mangyaɗan yaya kenan? Wace amsa take da shi na kare kanta. Dama tausayin yaron nan ya samu tasowa mu biyosa da wuri kafin abin yay zurfi. Amma tunda hakane zamuje muma har sai kun yanke hukunci kafin sannan shima Yaya Ibrahim ɗin ya dawo da ga tafiyar da yayi”.
Kuka mai tsuma rai Sa’id ya saki, dan harga ALLAH yana matuƙar ƙaunar matarsa Hauwa’u da ƴar ɗiyarsu Nasreen da taci sunan mahaifiyar tasa. Amma hukuncin da iyayen nasa suka yanke yasa bazai iya jayayya da su ba. Babu yanda zai yi ya bisu yana kallon Hawwah da kanta ke ƙasa tun shigiwarta batako kalla sashen da yake ba ma……
Ajiyar zuciya Abba ya saki a hankali, kamar zai yi magana sai kuma ya fasa. A taƙaice ya ce, “Kuje ciki zamuyi maganar a nutse”. Daga Hawwah har Smart miƙewa sukai suka fice. Babu kowa a tsakar gidan sai Umma da ke kai kawon girkin rana. Yanda bata tanka musu ba suma basu tanka mata ba. Sai dai murmushin data saki akan idon Smart. Shi ba ma’abocin maida hankali bane akan irin waɗan nan abubuwan dan haka yay shigewarsa, sai dai murmushin ya sosa masa zuciya da tsaya masa a rai. Ammah dake zaune a falo Nasreen a cinyarta tana shan kunu kallo ɗaya tai musu ta maida hankalinta ga Nasreen ɗin. Zama yay kamar yanda Hawwah da ke sharar hawaye itama ta zauna. Idanu ya ɗan zuba mata tare da furzar da huci kaɗan. “Shi wannan kukan babu amfanin da zai miki, bakuma zai gyara abinda yake faruwar ba. Kisama ranki haƙuri da nutsuwa, dan bazaki koma wannan gidan ba har sai tasan darajarki. Idan kuma kina ganin ba’ai miki gata ba a hakan dan naga k da mijin naki duk shashashu ne ga hanya nan zaki iya binsu” Daga haka ya miƙe.
“Kayi haƙuri Yaya ni banga laifinka ba, kuma nagode da ƙoƙarinka a kaina”.
Komai baice mata ba, sai duban Ammah da tai kamar bata ɗakin da yay. “Ammah ni zan koma”.
“ALLAH ya tsare ya bada sa’a”. Tace masa batare data ɗago ba. Da Amin ya amsa yana ɗan lakatar kumatun Nasreen da itama tai masa a dawo lafiyar. Da ga haka ya fice abinsa badan yasan ina ya kamata ya dosa ba tunda boss ɗin tasa ta korosa yau.
Sai da ya fito gaba ɗaya da ga layin nasu zuciyarsa ta kwaɗaita masa zuwa ma ya duba trainers ɗinsu. Dan kwana biyu basuga juna ba. Waya ya ciro tare da ɗan ƙura mata ido kamar mai tunani, sai kuma ya ɗan ɗage kafaɗa tare da kai wayar kunnensa bayan yay dailing number daya lalubo. Bugu uku aka ɗaga, yay ƙaramin murmushi da faɗin, “Barka da hantsi sir”. Amsar da aka bashi da ga can ta sakashi sakin murmushi. Sai kuma ya ɗan shafo kansa alamar jin kunya tamkar yana gabansa. “Am sorry Sir na ɗauka laifina. Yanzu ma ina son zuwa gaishekanne shiyyasa nace bara naji inda kake”. Ya ɗan yi shiru alamar saurare. Sai kuma ya amsa da “Okay gani nan zuwa in sha ALLAHU”.
Tafiyar mintuna ƙalilan da bai wuce ashirin ba ta kaisa babban stadium ɗin da coach ɗin nasa yace masa yana acan. Wajen ya ƙayatu matuƙa. Babu yawan hayaniyar mutane sai isu-isu ƴan wasa da ke ta tsalle-tsalle alamar training sukeyi saboda wasan sada zumunci da suke shirin zuwa kudancin ƙasar. Tunda ya shigo wajen ɗaya da ga cikinsu da ya fara ganinsa ya saki wani irin fito daya jawo hankalin sauran suma. *_“Capten!! Carpten!!”_* suka shiga faɗa cikin ihun da ke nuna tsantsar farin cikin ganinsa. Murmushin Smart ne ya sake faɗaɗa, shima ya shiga ɗaga musu hannayensa duka biyu har ya ƙarasa gaban Trainers ɗin nasu da ke kallonsa shima da murmushi. Har cikin rai yana matuƙar son yaron, ya kuma ci buri a kansa dan Smart ya iya gara ƙwallo mai suna ƙwallo ta gaske, dan ma mun kasance a ƙasa irin ta Nigeria da mai alfarma yafi ma’iyi da tuni wani labarin ake akansa ba wannan ba. Amma duk da haka shima ya damu wasu dama na barin ƙasar ƙaddara ta toshe su. Sai dai ALLAH mai hikima duk da tarin damammakin da yaron ya samu tun yana da shekara goma sha takwas komai yaƙi motsa kansa a inda yake. Hannunsa ya kamo da ga hanashi risininawar da yay niyyar yi, “Yarona irin wannan ƙiba haka anya kuwa kana motsa jiki?”.
A yanda coach ɗin yay maganar ya saka Smart yin ƙaramar dariya da shafa kai yana ɗan dudduƙar da kansa da faɗin. “Sir ina nan a yanda ka sanni girman rigane kawai”.
“Bari nace to. Amma badan na yarda ba. Ykk to ya kwana biyu? Tunda ka samu aikin nan ka ɓuya gaba ɗaya ko?”. Ya ƙare maganar yana jan hanunsa suka ƙarasa kan wasu kujeru da ke gefe kaɗan. Smart da har yanzu bai bar murmushi ba ya ce, “Sir aikinne bai barin motsin kirki. Amma kuna raina sosai”.
“To Alhamdullah babu dai wata matsala kuma ko?”.
“Da sauƙi dai Sir”.
“A cigaba da haƙuri, komai yay farko zaiyi ƙarshe. Fatanmu dai ALLAH ya warware mana abinda bamu da ilimin sani akansa”.
“Amin Sir”. Ya faɗa cikin damuwa idanunsa akan teammate ɗinsa da ke ta tsalle-tsalle su har yanzu. Hira suka cigaba da yi da oga wani kaso na hankalinsa na ga teammate ɗin nasa dai. Kiran wayar coach da akai ta sakashi miƙewa ya ɗan matsa a wajen. Dai-dai nan ɗaya daga cikin ball ɗin da suke training ɗin da ita ta gangaro wajen filin har inda Smart ke zaune. Kamar wanda aka tsikara ya miƙe da alamar tsumin ya motsa. Cikin wani irin salo da iya ƙwarewa a harkar ya buga ball ɗin tamkar abin almara bata sauka ko ina ba sai cikin raga. A take wajen ya ruɗe da ihunsa, kamar waɗanda ake juyawa da remote suka raba kansu yanda ƴan ƙwallo kanyi a cikin fili yayin wasa. Ƙarasa shigewa cikin filin yay shima cikin zafin nama da jin shauƙi a ransa, dan da gaske ball itace hubby na Smart. Tana sakashi karsashi da nishaɗi maƙurar ƙurewa.
Juyowar coach da ya kammala waya ya sashi waro idanunsa waje sosai na ganin abinda ke faruwa. Sosai ya rikice dan yasan da wahala a wanye lafiya… Ilai kuwa kafin ya kai ƙarshen tunaninsa da yay dai-dai da sake saka ƙwallo ta biyu a raga da Smart yayi ya wani ƙwalla ƙara hannayensa duka biyu dafe da kansa. Kafin su isa kansa ya zube ƙasa a sassanƙame. Hankalin coach idan yay dubu ya tashi, haka ma sauran teammate ɗin nasa duk sun rikice. Babu ɓata lokaci suka fiddashi a filin coach na musu faɗan miyasa suka barshi ya shiga tunda sun san matsalarsa. Su dai basu da tacewa dan mai afkuwa ta riga da ta afku kuma. Sai fatan a kiyaye na gaba dai.
Duk wani kalan taimakon da sukan masa idan matsalar ta samesa ita Hameed yay masa, sai dai kamar yanda aka saba babu alamar za’a samu kansa a yau ɗin. Sosai ya sake shiga damuwa, ina daɗi da ga zuwansa gaishesa a rarraɓesa a kaima iyayensa shi a haka. Dole yay kiran ƙaninsa Ahmad aboki ga Smart ɗin kenan akan yazo suje gidan su Smart ɗin. Da mamaki Ahmad ke tambayar yayan nasa ko wani abu ne ya faru? Bai wani tsaya kwana-kwana ba ta sanar masa. Hankalin Ahmad ya tashi, babu shiri ya baro office ya nufo stadium ɗin.
Yana ajiye wayar kiran babban amininsa Yousuf Ibrahim Jiƙamshi na shigo masa a waya (Uncle Yousuf) kamar bazai ɗaga ba sai kuma ya ɗaga ɗin dan sunyi da shi zasu haɗu shi shaf ma ya manta sai da yaga kiran. Furucin Uncle Yousuf da ke faɗin, “To baban ƴan tamaula ALLAH yasa dai ka gama da yaran naka dan bana son zuwa nai zaman jiranka zan koma office saboda baƙi da nake tsumaye bayan azhar”.
Cikin damuwa coach ya ce, “Wlhy ni nama manta da da batun zuwan naka ina nan a rikice”.
“A rikice kuma a kan mi?” Uncle Yousuf ta faɗa cikin mamakin aminin nasa.
Shima amsa ya bashi da faɗin, “Wlhy Aliyu ne yazo mu gaisa fa na ɗan tashi amsa waya ban san yaya akai ba ya shiga cikin fili ka gansa nan sharɓan babu alamar rai tare da shi”.
“Ya Arrahaman! Aliyu dai Aliyu nawa Smart Mawashi?”.
Sai yanzu ma shi coach ya tuna ashe Aliyu a ƙarƙashin abokin nasa yake a yanzu. Dan haka ya bashi amsa da cewar, “Yess! Yes! Shifa wlhy”.
“Ya Salam gani nan a hanya”.
Kusan a tare Uncle Yousuf da Ahmad suka iso wajen. Kowanne ya fito a motarsa da sassarfa zuwa inda suke zagaye da Smart da ke kwance a ƙasa kansa bisa jikin coach da ke faman shafa masa ruwa yana fatan ya farfaɗo, dan bai son su kai shi gida a wannan yanayin musamman daya tuno irin tashin hankalin da Ammah ta shiga last da abin ya faru da shi. Har rige-rige ake tsakanin Uncle Yousuf da Ahmad, sai dai kowanne ya samu nasarar kai hannunsa jikinsa. Ganin yanda aketa faman saka masa ruwa babu alamar zai farfaɗo Uncle Yousuf ya cema coach “Hameed muje asibiti kawai dan banga alamar zai farfaɗo ba a hakan nan”.
Cikin damuwa coach ya dubesa shima da bashi amsa da “Yousuf zuwa asibitin nan babu abinda zai canja. Dan mun gwada yin hakan a baya sai dai mu gama zaman banza dan su amsa ɗaya ma suke bamu zuciyarsa ta tsaya da aiki. Al’amarin nasa ne fa kamar abin sihiri gashi nan dai. Gida kawai ya kamata mu kaisa duk da gaskiya hakan na sakani fargaba dan tayarwa iyayensa hankali kawai zamuyi”.
“Gaskiya kar a kaishi can Brother” Ahmad ya faɗa cikin damuwa. Bai jira cewar kowa ba ya cigaba da faɗin, “Mizai hana muje wajen mutumin nan da ya taɓa bashi magani sanda abun ya takura masa”.
“Shawara mai ƙyau Ahmad, da ni duk nama rikice wlhy hakan bai zo min a rai ba. Kunga ku kamashi kusa a mota”.
A bayan motar Uncle Yousuf aka saka shi kamar yanda ya buƙata, shi da coach suka shiga gaba Ahmad a baya ya riƙe Smart. Kai tsaye ƙofar ruwa suka nufa, gudun da coach keyi ya sakasu isa cikin ƙanƙanin lokaci. Gidane irin na talaka mai ƙaramin ƙarfi, sai dai da ga waje shafe yake da siminti tsaf da shi da milk ɗin fenti. Da ga gaban gidan kaɗan islamiyya ce ta ƙanan yara da keta karatu kasancewar akwai ta safe zuwa ƙarfe ɗaya. Tsaiwar motar ta saka wani saurayi da ke tsaye da ga jikin barandar Islamiyyar matsowa garesu yana musu sannu. Basu wani tsaya jan maganar ba suka buƙaci ganin Malam. Kafin ya basu amsa sai ga malam ɗin ya fito da ga gida……….✍️
_Yau dai Smart ɗin ku ya ɗan bani tausayi🥲_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣8️⃣
_Ya rabbi ka gafartama *Sheikh Abubakar Giro Arugungun*. Ka yafe masa kurakuransa, alkairan da ya isar garemu na wa’azantarwa da koyarwa kasa ya amfanar da mu duniya da lahira. ALLAH ya albarkaci zuri’arsa. Suma iyayenmu ALLAH ka gafarta musu, damu baki ɗaya 😭✍️_.
……..Wata nannauyar ajiyar zuciya Smart ya saki mai ƙarfin gaske lokacin da malam ya shafa masa ruwan addu’oi da yayi tofi a ciki, sautin karatun suratul Naazi’aat da ɗaliban malam ce ta fara shiga cikin kunnensa da wani irin ƙarfi tamkar a iya cikin kunnen nasa akeyi. Ya sake sakin ajiyar zuciya sai kuma ya kai hannunsa ya dafe goshinsa dan kansa wani irin ciwo yake kamar zai tarwatse. Uncle Yousuf ne ya fara ambatar sunansa, dan haka ya sake yunƙurin buɗe idonsa a karo na biyu sai dai ya kasa. A rikice duk suka dubi malam. Ya karkaɗa musu kansa da faɗin, “Kamar yanda na faɗa muku tun wancan karon ku sake jajircewa wajen addu’a da sadaka akansa, dan al’amarin nasa akwai ruɗani kamar na sihiri mai ƙarfi. Sai dai ban tabbatar ba dan UBANGIJI shine kawai masanin gaibu. Amma gaskiya al’amarin nasa yana nuna kamar bugewar junnu ne. Na fara baku ruwan addu’oi a wancan karon amma sai aka daina zuwa a karɓa kwata-kwata, dama ba komai bane face addu’oin karya sihiri wanda ya kamata ma ace duk musulmi kan dingayi a gidansa domin shi da iyalinsa koda lafiya lau ake dan rayuwa kake baka san mike biye da al’amarin ka ba. Koba sirihi akwai baki (kambun baka) da yafi sihiri kaifi a wasu lokutan. Koda ma bazaku juri zuwa nan ɗin a karɓa ba to ku dage da yi masa a gida dan ALLAH”.
A tare suka amsa da “In sha ALLAH malam” sai kuma suka ɗora da godiya. Ganin yanda Smart keta faman jujjuya kansa malam ya ƙara masa addu’a tare da basu umarnin kaisa asibiti mafi kusa. Godiya sukai masa dan a wancan karon ma haka yay musu. Suka ajiye masa sadaka shi kuma ya basu ganyen magarya da ayoyin da zasu karanta da ga cikin Alkur’ani mai girma. Kai tsaye asibitin suka nufa kuwa, inda aka bashi gado dan a kallo ɗaya idan kai masa dole ne ya baka tausayi, kai kace ba a yanzu kaɗai ya kasance a kwance ba yanda yay sharɓan. Sun bashi taimakon gaggawa har sai da ya samu barci suka ɗan samu nutsuwa. Sun yanke shawarar sanar da gidansu amma sai coach ya ce adai ɗan dakata idan basu sallamesa zuwa yamma bane sai a sanar musun. Hakan ya musu, dan haka sukai yunƙurin fitowa aka barsa da Ahmad ya zauna da shi kafin suje su dawo…..
★★★★★
Duk yanda taso cigaba da gudanar da al’amuran gabanta na wannan yinin hakan sai ya nema gagararta. Ba ƙaramin tsaya mata a rai abinda drivern nata yay mata yayi ba. Dole ta hakura da tattara bayanan case ɗin da zata fara tunkara a safiyar litinin kan dukiyar wasu marayu da wan mahaifiyarsu ke ƙoƙarin handamewa dan zuciyarta a cinkushe take matuƙa. Steering da take murzawa ta kaima duka a karo na babu adadi. Ta cije lips da masifar ƙarfi da faɗin, “Sai na koya maka hankali!”. Kalmace data ambatata yafi sau shurin masaƙi. Ga takaicin daren jiya da ma na cigaba da ci mata rai dan a duniya tai masifar tsanar wani namiji ya raɓeta da sunan taɓata ko soyayya. Shiyyasa shima Tajuddeen lissafinsa ya shiga cikin jerin lissafin abubuwa masu ƙuna da ajiyewa a kudin tarihinta na wannan yinin da take ganin yazo mata a birkice. Office ta koma, inda ta tarar da baƙi kashi-kashi na jiranta. Tabbas batajin magana, sai dai a ɓangaren aikinta ita ɗin jajirtacciya ce, dan ma ɗabi’arta ta shaye-shaye na matuƙar maidata baya a lokuta da dama, dan badan wata hikima ta UBANGIJI ba da Lulu ta jima da daina zuwa wajen aikin ma gaba ɗaya ne. Mummunar hallayya mafi muni tattare da Mawaddat shine sakaci da addini, sam babu abinda ta sani akan addininta sai abinda ba’a rasa ba sakamakon karatun ta na lawyer. Bata san a kira salla ta tashi tayita akan lokacinta ba, to idan ma tayin babu maganar yinta a yanda MANZON ALLAH ya koyar damu. (Kuyi haƙuri ba Lulu kaɗaice a wannan matsalar ba. Wlhy da yawan mutane sunayin salla ne ba’a yanda MANZON ALLAH ya koyar ba. Dan bawai fa muna nufin Lulu bata san salla ba, a’a itama ta tashi ne a yanayin yanda akeyi kawai nakeyi batare da samun ilimin yinta ba kamar yanda da yawa mutane suka kasance. Mafi yawanmu idan da zaman tsayawa akan ibadarmu ta salla za’ai tun daga tsaiwarta ma zamu fara samun gyara. Please Dan ALLAH a wannan gaɓar kowanmu ya nutsu ya kalla sallarsa da kuma bincike akan yaya ake salla kamar yanda MANZON ALLAH S.A.W ya koyar mu gani ko zamu ribantu da gyarawa). Sanda ta gadama take salla, tana kuma yin tane a yanda kawai taga anayi kasancewar karatun addinin ma gatan mahaifinta ya zame mata cutarwar da bata samesa ba. Masifarta kam wannan halitta ce, wani mai haƙuri wani saɓani haka. Sai ɗabi’ar shaye-shayen data jima tana binnewa wanda har yanzu bamu san tushen farawarta ba ko dalilinsa. Wulaƙanta mutane da takasu a duk yanda taso kuskuren mahaifinta ne da ya ɗorata a turbar komai take so zata samu. A duk sanda ka nunama yaro komai yake so zai samu tofa kansa zai ƙara girmane da tunanin yafi kowa daraja da power a rayuwa, sannan akan komai shine sama da kowa. (Iyaye sai mu kula hakan ba soyayya bace)….
Yanda ta zube wayoyinta da zama jagwab cikin lallausar kujerar office ɗin nata ya sake bayyanar da ɓacin ranta akan fuska. Hand bag dinta ta jawo tare da fiddo key ɗin drower ɗin jikin decks ɗinta da bata yarda kowa ya taɓa saboda abinda take ajiyewa a ciki ta lalubo. Tana ƙoƙarin buɗe drower ɗin sakatariyarta ya shigo office ɗin da sallama. Wani takaici ya sata ɗago idanunta da suka kaɗe da gajiya. Sai dai gaba ɗaya tama kasa mata masifar da ta saba yi mata a duk sanda tai mata kuskure. Da sauri sakatariyar ta ce, “Please am sorry maa. Wlhy abinda matar can tazo da shi ne yay matuƙar tayarmin da hankali. Jiya ma tazo nace mata ta dawo yau dan kina up 2days sai yau ne zakiyi res…..”
Hannu Lulu ta ɗaga mata alamar gajiya da saurarenta. Murya a shaƙe ta ce, “Zainab ba wanda zan iya saurare a yau koma minene akazo da shi. Ki sake bama duk wanda ya dace sabon appointment banda yau da gobe. Duk case ɗin da kuma kika sani bani da buƙatarsa a teburina karma mai shi ya shigomin office ok”.
Zainab da damuwa ta bayyana ma a fuska ƙarara ta gyaɗa kanta da ke ƙasa. Sai kuma cikin rawar murya dan har ta fara hawaye ta furta, “Aunty matar can fa mijinta ne yayma yarinyarta da taje agolanci da ita gidansa fyaɗe. Kuma yarinyar shekararta tara kwata-kwata. Sunje asibiti da yarinyar amma anƙi karɓarsu tun jiyan wai sai da ƴan sanda. Taje police station ɗin kuma ƴan sandan nata mata yawo da hankali. Wlhy bakiga a yanda sukazo da yarinyar ba a jiya da yamma abin babu ƙyan gani….”
Wani irin matse idanu da damƙe kujera Lulu da jikinta ya fara tsumar mazari tayi. (Mawaddat calm down. Mawaddat calm down. Mawaddat calm down). Wani sashe na zuciyarta ke ta ambata mata. Sannu-sannu ta fara sassauta damƙe kujerar da rumtse idanun nata da tai, sai kuma ta buɗesu gaba ɗaya sunyi jajur matuƙa kamar wadda tasha wani abu a lokacin.
“Shigomin da ita”.
Ta faɗa ƙirjinta na ƙara ƙarfin sukar da yake mata. Ga jikinta bai daina tsumar da yake ba. Da ace tanada ilimin addini da addu’a tafi cancanta da harshenta a irin yanayin. Amma sai aka samu akasin hakan a gareta. Da sauri sakatariyar ta ta fice cikin matuƙar sassarfa. Minti biyu basu rufaba sai gasu sun shigo. Matar dai da ka ganta kaga wadda ke’a cikin mawuyacin hali, sai dai da zata samu kulawa ƙyaƙyawar mace ce dirarriya. A lamarin Lulu da talaka a teburin aikinta kawai suke iya shan inuwa ɗaya, shima akan abinda ya shafi aikintane kawai babu ruwanta da rayuwarka. Har ƙasa matar ta kai ga alamun ciki da ya turo a jikinta zata gaida Lulu. Bata hanata durƙusawar ba amma dukkan hankalinta na gareta, sai kuma katseta da ga gaisuwar data fara da tai…
“Kinga wannan gaisuwar baida amfani faɗamin ina yarinyar take?”.
Cikin gyaɗa kai da share hawaye matar ta ce, “Tana gidan ƴar uwata da ta rakoni nan jiya, saboda yanda jikin nata yake ne ƴar uwar tawa tace na dawo yau ita ta kula min da ita”.
“Wane police station kukaje domin kai ƙarar?”.
“Na nan unguwarmu ne sai kuma da mukazo nan wajen ƴar uwar tawa itama ta kaimu na nan ɗin. Sai dai shima basu ɗauki abin da muhimmanci ba shiyyasa ta ce zata rakoni nan inda take da tabbacin za’a share mana hawaye. Hajiya dan ALLAH ki taimakeni kamar yanda ALLAH ya taimakeki. Yarinyar nan marainiya ce mutuwar mahaifinta ta sani auren wannan tsinannen da tunda na aure shi ban sake farin ciki a rayuwata ba……”
Cikin jan tsaki da takaici Lulu ta katseta da faɗin, “Kika zauna da shi kuma har ya miki ciki. Malama ni ba rayuwar aurenki nake buƙatar ji ba. Ki tashi kuje zan haɗaki yanzu da wanda zaku sameni a asibiti”. Ta ƙare maganar tana miƙewa cikin matsanancin ɓacin rai. Waya takai kunnenta, da ga can aka ɗaga. Kirari aka fara mata ta katse da faɗin, “Musa ka sameni a office yanzu kai da Shu’aibu Please inada emergency case.”
“An gama ranki ya daɗe”.
Musa ya faɗa ransa fes dan yasan yau aljihunsu zai kasance a cike. Dan aiki da Lulu yafi masa zaman cikin station aita kayan hamma balle tsaiwar kan titi amsar na goro. Ɗan rubutu tai a takardar data yago ta miƙama sakatariyar ta dake tsaye har yanzu. “Idan sun zo ki basu wannan, suje da ita sai su sameni a wannan asibitin dana rubuta. Kibasu 5k da zasu saka mai a mota”. Daga haka ta fisgi hand bag dinta da ɗayar wayarta da key tai waje…
Batako kalli sauran mutanen da ke zaune a inda table ɗin sakatariyarta ya ke ba ta fice. Taja ƙaramin tsaki lokacin da take dana unlock ɗin motar tunkan ta ƙarasa gareta. Bazata iya jure wannan zirga-zirgar tuƙin ba fa gaskiya. Dan tun farko ita dama ba gwanar sonyi driving bace. Cikin ƙara jan tsaki lokacin da take ficewa a gate ɗin ta dannama Uncle Yousuf kira. Sai da ta shiga ta tuna abinda ya faru jiya da wasan ɓuyan data ƙudiri aniyar farayi da shi. Da sauri ta rarumi wayar zata katse sai dai harya ɗaga. Babu alamar wasa a muryarsa ya ce, “Lafiya?”.
Kamar ta fasa ihu haka taji, amma sai ta dake cikin pretending da ƴar shagwaɓa ta ce, “Uncle Barka da safiya. Dama no ɗin mutumin nan zaka turamin koka kiramin shi Please ya sameni a Shira’s hospital”.
Ɗan jimmm yay kamar bazai amsa mata ba sai kuma cikin dakewar da takan bata tsoro a Duk sanda yayita ya ce, “Wane mutumin?”.
Yanzu kam sai da taji bugawar zuciya. Da ɗan rawar harshe ta ce, “Driver fa my papa”.
Har zaiyi yi mata tambayar yaya akai bashi ya kaita office ba sai kuma ya fasa saboda tare ya ke da abokinsa Hameed. “K kina ina yanzu?”. Ya faɗa cikin goce tunaninsa.
“Ina hanyar Shira’s hospital ɗinne ”.
“Sai kin ƙaraso”.
Ya faɗa kawai yana yanke kiran…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣9️⃣
……..Kaɗan ya rage ta bugama motar gabanta. Tai saurin take birkin da ƙarfi. Ganin yanda mai motar ya dakata shima da alama fitowa zaiyi ya sata sake mata key tabar wajen da saurin dan ba wannan ne a gabanta ba yanzu. Tana hango zagin da mai motar ke mata cikin daƙuwa da wanda wasu ke mata na gefen titi. Oho basu bane a gabanta. Furucin Uncle Yousuf ne ke mata kai da kawo. Ji take kamar ta koma su canja asibiti sai dai ta riga kuma tace su Sha’aibu su sameta a can. Sannan yanda uwar ke nuna yarinyar na cikin mawuyacin hali maganar sakaci daga gare ta ma bata taso ba, dan a yanzu al’amarin su drivern ta ya shafe a zuciyarta yanda zata yaga rayuwar mijin matar nan kawai take ƙullawa. A wannan fanin ba’a gayyacesu ba ma taka rawa suke balle sune da bikin. Ai rawa sai kalar wadda sukaso takawa wlhy…..
“Da gaske dai Uncle You na asibitin nan? To mi ha kawoshi?”. Ta faɗa a fili tana parking idanota akan motar Uncle Yousuf dan babu ta yanda za’ai motocin gidansu su ɓace mata. Cikin rashin sanin abinda take buƙatar sani ta fito a motar. Sai da ta leƙa motar Uncle Yousuf ta tabbatar babu kowa a ciki sannan ta bar wajen zuwa cikin asibitin. A reseption kuwa suka haɗu da Uncle Yousuf ɗin. Karan farko a rayuwa taji bazata iya haɗa ido da shi ba, tsoron ma haɗuwar tasu take yi. Musamman kuma yanda ya zuba mata idanun nasa duk sai ta nema daburcewa. Shi ya fara ɗauke idanunsa da ga kanta yana kai wayarsa da aka kira kan kunne. Hakan ya bata damar nufar inda ake yankar kati, sai dai kuma fa ko sunan yarinyar bata sani ba ma fa ashe. Cikin ɗan yarfar da hannu da juyawa gaba ɗayanta tai facing ƙofa ta ke faɗin “Ouhhh! Saurin banza ma ashe nake”. Dai-dai nan motar ƴan sanda mai ɗauke da matar nan da yayarta da yarinyar suka iso. Shigowar Musa ya sata sauke ajiyar zuciya, shi ya sanar da nurses cewar akwai mara lafiya a waje kafin ya ƙaraso gareta. Kallo ɗaya da Lulu taima yarinyar ya sata rumtse idanunta takalminta har yana gullewa sai da ta dafe kantar reseption ɗin…….
“★“★ ∆ ★”★”
“Ranka ya daɗe yaron nan fa daka tada hankalinka kansa ba wani ɗan kowa bane face wani mutum da ake kira Malam Mika’il Idris Mawashi a anguwar fagge. Shi kansa mahaifin nasa a iya layin nasu kawai aka sanshi balle shi. Kuma da gaske drivern yarinyar ne kwata-kwata bai ƙulla sati huɗu da fara aiki gidan Alhaji Isma’il Jiƙamshi b…..”
“Kace Alhaji wa?!!”.
Alh. Baita yay saurin tarar numfashin yaronsa da suke kira Goga a kamar razane da jin sunan Alhaji Isma’il Jiƙamshin. Bashi kawai ba hatta Hon. Nakowa da ke tare da shi dan tunda suka baro gidan MM Atik Kumo da ya basu aro anan gidan hutawar Alh. Baitan suka ƙarasa kwanan nasu. Shine tun da farar safiya kuma suka nemi babban yaronsu na bangar siyasa Goga suka sakashi binciko wanene Smart ta hanyar ɗan bayanai da suka samu ga Nadiya wadda itama ta samune ga Lulu randa taje saloon shagonta….
“Alhaji Isma’il Jiƙamshi nace ƙwarai da gaske oga. Dan shine mahaifin ita yarinyar ma ai.”
“Babbar magana ƴarsa ta cikinsa?”. Hon. Nakowa ya faɗa wani irin abu mai ma’anoni da yawa na tsirga masa tun daga saman kai har tsakkiyar ƙafafunsa. Cikin tabbatarwa Goga ya gyaɗa masa kai. Tare da masa ƙarin bayanin da zai gaskata hakan duk da shi bai san dalilinsu na jinjina sunan ba tunda shi dai a ɗazun yaga hankalinsu akan yaron yake ba ita yarinyar ba.
“Kaga jeka”.
Honorable Babale ya faɗa cikin katse masa tunani. Dai-dai Goga na miƙewa ya sake faɗin ka jiramu a waje nan zamu nemeka.” shi dai da to ya amsa musu ya fice kamar yanda suka buƙata. Yana kuwa fita Hon. Nakowa ya firta, “Tabɗi jan inji mata. Dama ƴar iskar yarinyar nan ɗiyar Isma’il Jiƙamshi ce? Haba shiyyasa bata zubar a banza ba.” sai kuma ya wani ƙyalkyale da dariya alamar hakan ya masa daɗi ƙwarai da gaske. Shima Alh. Baita dariyar ya fara. Sai kuma ya buga ƙafa da faɗin, “In kere na yawo zabo na yawo tabbas faɗar masu iya magana watarana za’a gamu. Honorable Please kira mana Hon. Misau mana. Dolene ai wannan shagalin da shi”.
“Ƙwarai ma kuwa”. Cewar Hon. Nakowa yana wani bula-bula da babbar riga wajen laluben wayarsa. Cirota yay tare da yin danne-danne ya kai kunnensa……
Tofa masu karatu wata sabuwa kenan. Mi’a haɗin Daddy kuma da su Honorables?🤔.
∆★∆★∆★∆
Tun bayan wucewar ɗan nasa yake ta faman kai kawo a lafiyayyen office ɗin nasa. Abubuwa da yawa ne ke masa sukur-sukur a brain game da buƙatar autan nasa a karo na biyu. Tabbas zai fi kowa farin ciki da ƙulluwar wannan auren dan koba komai dai Mawaddat ɗiyar ƴar uwarsa ce Mawaddat. Ƙanwarsa mafi soyuwa garesa a duk cikin ƙannensa. Wadda yasha bama sirrin al’amuransa batare da tunani ko jin ɗar ba har ALLAH ya ɗauki ranta. Zai kasance mai yin farin cikin ganin jininsa da nata sun zama abu ɗaya. Sai dai kuma matsalar itace Isma’il. Isma’il shine babban bakangizo mai razani da ya gitta a tsakkiyar wannan ƙaunar zumunta mai cike da ababen burgewa ga duk wanda zai iya jin asalinta da wanzuwar ta. Dan tarihin ratsawar Isma’il a cikin labarinsa dana ƴar uwarsa uwa ɗaya uba ɗaya ya juya akalar waccan ƙayataccen labarin zuwa ɗimautacce mara armashi a yanzu. Ata wani fanin kuma kamar zai zo da sabon armashin kansa da kansa dan labarin zai canja ne da ga na shi da ƴar uwarsa zuwa na shi da Isma’il Ibrahim Jiƙamshi mijin ƴar uwarsa da ƴarsa. Ƴarsa da yasan yana matuƙar ƙauna fiye da komai a rayuwa. Kafin yau da faruwar matsalar farko na tusguɗewar aure tsakanin Mawaddat da Tajuddeen labarin ba a haka ya tsarashi ba, sai dai yana ganin wata dama ce da zai masa editing dan ya zauna dai-dai da zamanin nan na 2023 a ajiye wancan ƙarnin dan ya koma tsohon yayi. Ya wani lumshe idanu da dunƙule hannunsa ya ce, “Yess!! Sulaiman Sufi Ado Garko kai mai nasara ne akoda yaushe. Isma’il Jiƙamshi sabon game, sabbin players and sabon stadium ka zama cikin shiri”.
Wata sabuwar kuma dai🤔.
★★★★★
Duk da a yanda take jin matuƙar gajiya bata huta ba har sai da doctors suka rufu akan yarinyar nan da lamarinta ya taɓa duk wanda ya ganta a cikin asibitin. Dan hatta Uncle Yousuf tuni ya ajiye batun takaicin Lulu gefe da shi akai komai na ganin likitoci sun tsaya a kanta. Abin tausayi ita uwar ma zuciyar ta bushe ko kukan zahiri ta kasa sai na zuci. Ganin komai ya natsa dan ana neman uku na rana ma Uncle Yousuf ya kai dubansa ga Lulu da alamunta suka nuna gajiyarta matuƙa. Dan sai faman yamutse fuska take. Tausayi ta bashi, dan haka ya cigaba da kallonta a kaikaice cikin tausasawa da mata addu’ar shiriya akan halayenta marasa ƙyau. Isowar Ahmad wajen ta sakashi maida hankali garesa. Fuskarsa da murmushi yay ma Lulu magana, amma sai ta amsa masa a ɗan ɗage. Bai damu ba dan ya santa ya san halinta. Hasalima ya taɓa nuna sonta amma ta taka masa burki lokacin tana farkon dawowarta da ga Uk. Uncle Yousuf da yanda tai masa ɗin ya bashi takaici ya harareta, sai kuma ya maida hankalinsa ga Ahmad ɗin da ke faɗin, “Yaya ya farka, doctor ɗin ma ya sallamemu dan ya matsa zaije gida. Kasan Mawashi fa sam bai son asibiti.”
Murmushin Uncle Yousuf yay, cikin yanayin tsokana ya ce, “Kai haba kamar wani yaro ko mace”.
Dariya Ahmad yayi, dai-dai nan Smart ya fito a wani ɗaki da ke kusa da inda suke. Coach riƙe da hanunsa kamar wani ƙaramin yaro sai ɓata fuska yake. Dan da gasken fa bai son asibiti shi sam a rayuwarsa. Kuma bai san allura. Yanzu ma ba ƙaramar badaƙala akasha ba kafin ai masa shine ma Ahmad yay fushi ya fito. Ilai kuwa hararar Ahmad ɗin yayi tare da ɗauke kansa duk a lokaci guda, cikin rashin sa’a ya saukesu akan Lulu da tai kicin-kicin da fuska saboda kasancewar Ahamd a wajen, ita ala dole kar a kawo mata raini, dan duk wanda ya taɓa furta cewa yana sonta ko ya nuna basa ƙara shan inuwa ɗaya kuma. Ƙoƙarin janyewa yake sai kuma yay dai-dai da ɗagowarta cikin shirin miƙewa tabar wajen. Ta wani yamutse fuska fiye da yanda take sai kace wadda taga kashi. Shima ƙara tsuke tashi fuskar ya ɗanyi tare da ɗauke kansa gaba ɗaya irin bai ganta ɗin nan ba ma….
“Ga Aliyu nan babu lafiya sai ki masa sannu. Dama ina son ki gama da wannan kai kawon ne muje ki dubashi ashe ma zasu sallamesa yanzu”. Uncle Yousuf ne yay maganar cikin katse hanzarin Lulu dake niyyar barin wajen abubuwa masu yawa na mata kai da kawo musamman ganin drivern nata a nan. Dakatawar tai, sai dai ta kasa cewa komai sai ɗan hararsa da take ƙasa-ƙasa.
“Wai nikam bada Mawaddat nake ba?!”. Uncle Yousuf ya faɗa cikin ɗan kaushin murya dan ya san taurin kanta na tsiya da gadara. Sosai taji haushin hakan, amma babu yanda zatai dan Uncle Yousuf ne. Ta ɗan sake ɗagowa ta kallesa, a taƙaice ta furta, “ALLAH ya bada lafiya”.
Coach ne ya amsa da “Amin”. Cikin murmushi. Shi kam a zuciya ya amsa mata. A zahiri kam ya ɗauke kansa gefe kamar bai san da shi take ba. Sosai ta sake tunzura da salon rainin nasa. Tana mai tabbatar ma kanta a zuciya sai ta koya masa hankali da sauke masa wannan girman kan nasa. Batare da ta sake kallon kowa ba ta ce, “Uncle You ni na koma Office. Uncle Hameed ka gaidamin Aunty Rukayya sai nazo gaisheta”.
Coach yay ɗan murmushi da faɗin, “Zan sanar mata idan da gaske kike Daughter. Dan na sanki ke da sabgoginki marasa ƙarewa.” karan farko da ta saki sassanyan murmushinta da kan ƙawata ƙyawun fuskarta, sai dai batayinsa sai ta gadama. Kai Ahmad da zuciyarsa tai wani irin tsargawa ya ɗauke gefe. Dan Lulu cikakkiyar mace ce da kan iya jan hankalin mafi yawan maza musamman irin matasanmu na yanzu masu fifita ƙyale-ƙyale ga mace fiye da nagarta. Sai kuma ka kwasa ka kai gida ka samu fanko ce ko addininta bata sani ba sai duniyar kawai aka saka a gaba da son birge al’ummar cikinta….
Suma a tare suka fito su huɗun, Coach da Ahmad da Smart suka shiga motar Ahmad da ya koma ya ɗakko. Uncle Yousuf kuma ya shiga tasa motar dan Lulu kafin su fito ma har ta bar asibitin. Babu wanda ya sake bi takanta. Godiya Smart yay ma Uncle Yousuf sosai tare da su coach ɗin ma gaba ɗaya. Da ga haka kowa yaja motarsa. Har gida suka kaisa. Ahmad yay masa rakkiya har cikin ɗakunan kasancewar ba baƙonsa bane ɗakin dama. Bai wani zauna ba saboda Yayansa dake jiransa a mota. Yay masa ALLAH ya ƙara lafiya ya tafi…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣0️⃣
…….Bayan yay sallar la’asar barci ya sake sha har kusa da magrib batare da kowa yasan yana a gidan ba. Dan sanda su Ahmad suka maidosa basu ga kowa a ƙofar gida ba. Wanka yay da alwalar magrib ya fito. Yanayin yanda yake jin jikinsa babu ƙarfi ya sashi yin sallarsa a ɗaki. Bayan ya idar ya fita zuwa cikin gidan. A kallo ɗaya zaka iya fahimtar baida lafiya ƙarfin hali ne kawai. Sai dai hakan bai hanashi leƙa duk ɗakunan gidan ya gaida su Mama ba. A ɗakin Umma ya samu babban yayansu Salim yazo gidan shima. Sama-sama suka gaisa Salim ɗin na wani cika da batsewa shi adole mai naira a gida. Ko’a jikin Smart dan shi ba wannan shirmen ne a gabansa ba. Yana juya baya zai fita Salim ɗin da Umma suka raka bayansa da harara. Oho baima san sunai ba shi dai.
A falo ya samu ƙannen nasa duka. Sai Nasreen dake ta faman tsalle-tsalle ita da autar Aunty Amarya. Gaisheshi suka shigayi, ya amsa yana zama tare da ɗan dafe kansa da har yanzu bai gama saki ba. Ammah da tun shigowarsa take kallonsa ta ajiye littafin addu’oin da ke a hanunta da faɗin, “Baka da lafiya ne Hydar?”. Hannun ya janye da ga goshinsa ya ɗan furzar da iska. “Kaina ne ke ɗan ciwo kaɗan kawai Ammah, na kuma sha magani ma. Ina yini”. Maimakon amsawa sai ta cigaba da kallonsa cike da nazari. Ganin yanda ta kafesa da ido ya sashi duban Hawwah cikin son kauda hankalin Ammah ɗin ya ce, “K babu wata damuwa dai ko?”.
Kanta ta jinjina masa itama da ɗan damuwar ganin yanayin nasa. “Ba komai Yaya Hydar. Sai dai kamar ba ciwon kan bane kawai ke damunka. Ka wani zabge a lokaci ɗaya kamar wanda ya kwanta ciwo.”
Baiyi mamakin jin furuci nata ba. Dan a duk lokacin da ciwon ya bugesa ba ƙaramar fyaɗa yake masa ba. Ya ɗan sake furzar da iska yana tashi zaune da ƙyau da kamo hannayen su Nasreen. “Ciwon kai ne kawai kin san bai min da wasa”. Badan sun gamsu ba dai suka yarda da hakan. Maryam ce ta kawo masa abinci da faɗin, “Ko sai kayi sallar isha’i”.
Nan ma iskar ya ɗan furzar da duban kular abincin. Yasan dai shinkafa ce dan ya ga Salim na ci a wajen Umma. Shi kuma sam shinkafa bata da farin jini a wajensa sai dai kawai ya cita dan yunwa. “Ai banama jin zanci abincin nan ɗauke kawai. Ko kuna da ƙullin kamu ki ɗan dama min kaɗan”.
“Eh akwai. Dama na kunun gyaɗa da Ammah tasa aka markaɗo ɗazun ko shi za’a dama makan”.
“Yauwa dama min shi ɗin kawai bara naje massalaci na dawo”…
Ana idar da sallar isha’i ya sake dawowa. Anan yasha kunun gyaɗar da Maryam ɗin ta dama masa Ammah harda badawa a sayo masa ɗanyar awara dan tasan yana so sosai, kasancewar bata da yawa duk kafin ya dawo har an soya. Kusan ma tare suka cinye awarar da Nasreen da ke ta faman zuba masa surutu. Murmushi kawai yake mata cikin ƙarfin hali. Ammah dai da ke ɗan kallon tv duk tana lure da shi. Cikar agogo ƙarfe tara yasa Amma maida channel zuwa NTA, su Maryam ba wani son kallon labaran suke ba sai dai dole. Musamman ma Asma’u. Tashi yay ƙoƙarin yi shima sai dai kanun labaran suka ja hankalinsa. Inda rahoton farko ya kasance akan yanda shari’ar matashin nan Emanuel da aka kama a anguwar Yakasai akan lalata yara ƙanana maza da ya ɗauki tsawon shekaru uku yanayi. Kusan wata huɗu kenan ana tafka shari’ar sai a yau ne aka yanke masa hukuncin bisa jajircewar lawyer ɗin da ke tsaye akan bibiyar hakkin yaran da al’amarin ya shafa. Har tsakkiyar kansa yaji saukar muryarta tamkar a gabansa take kamar ko yaushe. Yanda take magana cikin nuna takaici da kuma jin daɗin samun nasara a shari’ar ya sashi kasa ɗauke idonsa ga tvn. Tambayar da ɗan jaridar yay mata akan miyasa a duk irin waɗan nan cases ɗin in dai tana a cikinsa da wahala bata samu nasara ba, anya ba tana saye bakin alƙalan bane ba ta bayan fage.
Ƙaramin murmushi da ke sake fidda loɓawar kumatunta duka biyu ta saki tare da yamutse fuska kamar yanda ya santa musamman idan tanajin masifa. Cikin izzar nan tata ta bama ɗan jaridar amsa da faɗin, “Mi zaisa sai na sayi alƙali akan abinda yake gaskiya. Ashe ma karatun da nai akan harkar shari’a da wahalhaluna sun zama a banza kenan in har sai na sayi alƙali akan gaskiya ta. Nasarata itace gaskiyata. Dan bana tsayawa mutum sai na tabbatar da gaskiyarsa. Na kumayi alkawarin cigaba da yaga mutunci da rayuwar duk wanda ya kasance bunsuru mai halayen dabbobi akan mutuncin yaran mutane. Dan ni duk wanda zai iya ƙwatar mutuncin yarinya ta ƙarfi ballema wadda take ƙanƙanuwa bashi da wani suna a gareni face Dabba alade. Yanzu shi wannan da na kai ƙasa ma ai yafi matsayin alade a gareni bamma san mizan kirashi ba. Shege ya baro yankinsa yazo yana ɓarna a namu yankin saboda suna ganin muna haihuwar yara mu saki a titi kamar bamu san ciwonsu ba. Indai akan harkar fyaɗe ne nai alƙawarin ni Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi sai na hana waɗannan aladun shan ruwa da numfashi cikin salama. Dan nan gaba kaɗan abinda suke lalata yaron mutanen da shi zan koma datsewa da almakashi ƴan ƙaniya. Idan aure kuke so uwarmi kuke jira da bazakuje kuyi ba ko ku tafi gidajen karuwai Mtsowww!!”.
Ɗan jaridar ya ce, “Turƙashi. Da alama dai Barrister Mawaddat Jiƙamshi ta fusata a wannan karon, masu halin binsiraye sai ku kama kawunanku, inba haka ba za’a sake maimaita gilli da girma bayan wanda akasha da ƙanƙanta. Sai dai a yayin da wannan zantuka na Barrister wasu ke nuna goyon bayanta wasu ƙalubalantarta suke musamman akan zance gilli da zata fara da kanta. Dan haka a yinin yau zantukan barrister suka ɗauki ɗumi da zagaye kafafen yaɗa labarai harma dana yanar gizo aketa tafka mahawara. Ballema da wasu ƙungiyoyin mata masu yaƙi da wannan ɗabi’a ta fyaɗe suka fito muraran da cewar sumafa suna bayanta. Dan zasu sayi nasu almakasan su fara sakawa a jakuna dumin tayata aikin gillin. To ALLAH dai ya ƙyauta, kowa rai yayma daɗi ai baran mai shi ne. Shi dai wannan gashi zai ƙare shekaru talatin cif a gidan kaso bisa tasa mummunar aƙidar mai muni, tare da biyan maƙudan kuɗin da za’a fuskanci lafiyar yaran da ya ɓatama rayuwa”.
“ALLAH yay ma wannan yarinya albarka da iyayen ma da suka kawo ta duniya”.
Furucin Ammah a bazata ya maidosa hankalinsa. A tare Hawwah da su Asma’u suka amsa da amin. Har Asma’u na faɗin, “Ammah nima in sha ALLAHU lauya zan zama. Wlhy tun randa na fara ganin matar nan kan case ɗin nan nake jin ƙaunarta da sha’awar nima na zama kamarta…..”
(Ba Amin ba a ɓoyayyar halayyarta) ya faɗa a zuciyarsa yana miƙewa batare da ya ƙarasa jin zancen Asma’un ba. Sallama yay musu ya fito acewarsa zai sha maganin ciwon kai ne ya kwanta. Sun masa addu’ar samun lafiya, yayinda Ammah ta dakatar da shi da faɗin yazo ta kama masa kan. Gabanta ya dawo ya zauna. Ta kai hannun nata saman goshinsa da ke da ɗumi har yanzu. A hankali ya sauke ajiyar zuciya da har ta iya jiyosa, sai dai batace komai ba dan tun ɗazun zuciyarta ke bata kodai lamarin nasa ne ya motsa bai son faɗa, ko kuma yana son ya motsa ɗin. Sosai tai masa addu’a yanata faman sauke ajiyar zuciya kafin ya miƙe yana jin wata nutsuwa ta musamman na ratsa masa jini da ɓargo. Koda ya koma ɗakin ma magungunan da malam ya bashi ya shashsha sannan ya kwanta. Maimakon barcin sai abinda ya gani a tv ya shiga dawo masa tiryan-tiryan. Shi yama rasa a mizai fassara wannan yarinya. Ita dai gata nan rabi mutum rabi muna mutum. Sai dai kalaman nata na yau sun matuƙar tasiri garesa har yana haɗasu da na jiya data dinga faɗa cikin shirmen buguwar ita ba ƴar iska bace. Bawai ya gamsu da hakan bane. Dan babu ta yanda za’ai irinta mai ƙwalewa da kayen maye ta iya furta ita ƙillatacciya ce ya yarda. A yanzu hakan ma wani sashe na zuciyarsa na kallon kalamanta na ɗazunne kawai a gurbin fuska biyu irin na halayyar ɗan adam na yanzu. Ya ɓoye zahirinsa na mutumin banza, ya shiga gaba-gaba wajen bayyanama duniya shi na kirki ne na ALLAH. Guntun tsoki yaja da lumshe idanunsa yana fatan barci ya ɗauke sa…..
★★★
★.★.★★
Tabbas a daren jiya yanda yaga rana haka yaga dare dan ko sau ɗaya bai rintsa ba. Sai faman bulbulama cikinsa hayaƙin cigarette da yay tayi dana shisha. Baya taɓa neman abu ya rasashi, haka ma bai taɓa harar mace sau biyu ba ta zille masa sai a kanta. Duk da ɓacin ran da ya tsinta kansa dalilin rasata a jiya bai ji ko ɗigon sha’awarta ya ragu masa a rai ba. Sai ma ƙaruwa yay yana sake azalzakarsa da sake tunzura buƙatarsa. Neman hanya ta uku ya tsunduma a tunani, sai dai zuciyarsa ta rabu gida biyu. Ɗaya na tabbatar masa ya nema aurenta kawai itace hanya mafi sauƙi. Ɗaya na tabbatar masa bazata amince ba, dan haka kota halin ƙaƙa kawai ya kore ƙishirwarsa, kai koda sakawa a sace masa itane. Ganin ya rasa makamar riƙewa sai kawai ya yanke shawarar neman shawarar abokinsa. Gabanin asuba yay kiransa, bugu biyu kuwa aka ɗaya dan shima a lokacin yana cikin club ne a Abuja……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣1️⃣
………“Mtsoww! Kaifa baka da aiki sai gantali, a ina kuma kake haka irin wannan lokacin?”.
“Kai mai maganar a ina kake? Kujimin sa ido. Kodan kaje Kano kai ka koma ɗan gargajiya”.
Ƙaramin tsaki Mm atik yay da faɗin, “Ɗan iska banda time ɗinka. Nifa magana mai muhimmanci na kira muyi, ka ɗan fita gefe Please nasan kana nan nane da cingam gal ɗin nan taka”.
“Naji, na matsa ɗan shiga sharo, ina saurarenka”.
Ɗan tsaki MM Atik yayi, dan harga ALLAH ya tsani budurwar abokin nasa da tabi ta kanainayesa ta hanashi rawar gaban hantsi. Cikin ture batunta ya ce, “Akan yarinyar nan ce dana faɗa maka. Plan ɗin mu na jiya fa ya rushe bata shiga tarkon ba”.
“Whart! Wai kana nufin ka aiwatar?”.
“Eh mana yau ɗin nan ma, amma sai…..” ya zayyane masa komai da ya faru. Da ga can Arman yay ƴar dariya da faɗin, “Wai driver? To ko dai shima yana hutawar ne?”.
“Mtoww bana jin hakan gaskiya. Dan randa na fara haɗuwa da ita na gansa. Yanda ta yarfashi ma sai ya baka tausayi. Kawai dai irin mutanen nan ne masu shegen shishshigin tsiya. Nidai yanzu manta bani mafita”.
“Ni dai mafita ɗaya na hango maka nasan kai kuma baka buƙatarta”.
“Waccece? Please tell me!”.
“Aure!”.
“Mtsoww auren ƙaniya. Nima ina tunanin haka, sai dai banda shiri gaskiya na zama da mace yanzu, ban san takura kai ma ka sani….”
“Ka tsaya nakai ƙarshe mana”.
“Oh sorry ina jinka”.
“Abinda nake nufi bawai auren nata zakai ba. Tunda ka riga ka ƙwallafa ranka ka zama cingam boy kuma ita bazata samu ta sauƙi ba kawai kasa su Dad gaba aje maka neman aurenta…..”
“Baka da hankali! Dad fa? Kasan waye Dad kuwa?!”.
“Calm dawn mana my man. Lamarin fa duk lissafine. Yanda Dad keda alfarma na tabbatar sun san juna da babanta tunda kace itama ƴar manya ce. So da zarar magana ta shiga kai kuma sai kaita jan ra’ayinta harka samu cikar burinka. Daga haka mu ƙirƙirar mata laifin da shi Dad ɗin da kansa zai ce bazaka aurenta ba”.
“Woow! Woow woow my dear wannan salon yayi kuma zai ƙayatar. Sannan ita kanta zan firgita lissafinta tasan ba irinmu ake ja a ƙasa ba. A safiyar yau ɗin nan zan zauna da Dad, nasan zai matuƙar ɗaukar abin da muhimmanci tunda dama burinsa kenan shi da Mom. Kai dai ALLAH ya barka da cingom gal taita ƙarar maka da ruwan kai bye”. Ya yanke wayar yana wani jin matuƙar farin ciki tamkar ya samu Lulu ƙamshi ɗin ya gama ne.
Ni ko na ce, “Hummm!”
★★★
Kamar yanda Alh. Baita da Hon. Nakowa suka girgiza da jin Mawaddat ɗiya ce ga Alhaji Isma’il Jiƙamshi haka shima Hon. Misau yay matuƙar girgiza da batun. Dan abune da ko’a lissafin hasashe basu taɓa kawowa ransu ba. A take suka zauna teburin shawara. Dan kuwa tabbas wata dama ce a yanzu tazo hannunsu akan Alhaji Isma’il Jiƙamshin. Kuma lokaci ne na ɗaukar fansa da zai goge tarihin baya labarin yazo da salon alƙalamin da sune zasu zama masu rubuta shi.
Tsaf suka kammala tsara komai a yanda suke buƙata. Fatansu kawai nasara da kuma sake sabon bincike dan ƙara riƙe hujjoji masu ƙarfi musamman akan Alhaji Sufi Garko da suka yanke shawarar tunkara a farko. Dan tabbas babban ɗaurin huhun goro suka shirya yima uban da ƴar gaba ɗaya dan su kasance gaba ɗaya a tafin hannunsu. Basu sa wasa ba tun a ranar suka nema appointment ɗin ganawa da babban ɗan kasuwar, kuma ƙusa a ɓangaren siyasar arewacin kasar musamman ma Kanon ta dabo Alhaji Sufi Ado Garko. Tsoho da kuɗi kenan abokin tafiyar yara, manyan kuwa baba suke kiransa dan ya kere ya kuma zarce koda a tsaransa. An tabbatar musu yaje Umrah sai dai nan da kwanaki biyu idan ya dawo washe gari su shigo. Sun samu wannan damar ne dalilin shaƙama babban yaronsa kuɗaɗe masu kauri, sai kuma mulki da Hon. Nakowa da Hon. Misau ke riƙe da shi wannan ma babban makami ne…..
★★★….
Ga Alhaji Sulaiman Sufi Garko ma ya gama shiryawa tsaf domin tunkarar mahaifin nasa game da auren Tajuddeen da Mawaddat. Dan a wannan karon ya ɗau aniyar koda yardarta, ko babu sai wanan auren ya ƙullun. Dan ya gama tanadar kalaman da zai tsara mahaifin nasa da su tsaf komai ya tafi dai-dai. Tajuddeen ya samu cikar burin shima ya samu nashi…..
★★★….
A ɓangaren Lulu ƙamshi da bata san mi suke ba gaba ɗaya hankalinta na kan case ɗin yarinya da akaima fyaɗe ne. Dan anata neman mijin matar amma an rasashi wai ya gudu yabar gari tun a randa yay abun. Wannan takaicin ne ya taru yay mata yawa ta tada hankalin su Sha’aibu ɗan sanda dama na duk wanda ke mata aiki idan irin wannan case ɗin ya taso. Hatta Daddy bata barsa ya huta ba. Ga takaicin Smart yaƙi dawowa aiki itako ta gaji da tuƙi dan sunata zirga-zirga. Shiko Uncle Yousuf ne yace ya zauna gida ya huta har sai jikinsa yay masa ƙarfi. A washe garin kwana na biyu da take saka ran dawowar Grandpa ɗinta da ga umra duk da tarin ayyukanta haka tai wancakali da su ta shiga tawagar ƴan tarbarsa a airport dan ya kwana biyu baya Nigeria, saboda daga uk ganin doctor ɗinsa ya wuce Saudiya Umrah. Tana kewarsa dan tana matuƙar so da ƙaunar kakan nata daya haifi mahaifiyarta da bata sani ba sai a hoto. Shi takema kallon uwa ga shi kuma shine kaɗai ya rage mata a kakanninta dama. Shima kuma a karan kansa yana nuna mata tsagwaron soyayya kasancewar ta ɗiya ga Mawaddat dinsa da ya rasa dan ita kaɗai ya taɓa rasawa a cikin ƴaƴansa shiyyasa yake matuƙar tausayin Lulu.
Ƙarfe kusan sha biyu jirginsu ya sauka. Duk da hango ƴan uwanta jikokin Alh. Sufi Garko da tai su Tajuddeen da sukazo tarbarsa suma ƙin fitowa tai tana daga motar har sai da taji ance jirgin da ya taso da ga Saudiyan ya sauka sannan ta fita. Sanye take cikin gawn ta material mai taushi da santsi da sukai matuƙar mata ƙyau da fidda mata ƙyaƙyƙyawar surarta kamar wata ƴar tsanar roba. Ɗaurin kanta da Amrah (Hussaina) tai mata yayi ƙyau ya kuma rufe mata gashi, sai ta gaba kaɗan da aka zamashi ake iya ganinsa baƙi siɗik a kwance, Kasancewar a ɗaure yake da ribbon sai yay tilluwa a cikin ɗankwalin da aka rufesa da shi ruf. Siririn mayafi kalar material ɗin ta ɗora a kafaɗa babu zancen yafawa. Sai dogon takalmi kamar koyaushe duk da kuwa ita ɗin doguwa ce amma bacan ba tsaka tsaki. Ƙaramar handbag ɗin hanunta ta sake gyarawa da gilashin idonta da ya sake ƙawata kwalliyar tata duk da kuwa a fuskarta babu ko ɗigon kwalliya bayan hoda dan itafa bata kwalliya, sai lips glose data saka a lips ɗinta kaɗan. Yanda take taku kamar wata tarwaɗa da sautin da takalmanta ke badawa ga ƙamshin turarenta data bulbula ya sata janyo hankulan mutane gareta musamman na kusa da ita. Sosai numfashin Tajuddeen ya dinga kaikawo a ƙirji har ta ƙaraso garesu. Ya haɗiye busashen yawun da ya kasa wuce masa a maƙoshi yana ɗan sakin murmushi. Ɗauke kanta tai kamar bata gansa ba, sai ma yatsu biyu data ɗaga musu a taƙaice tare da faɗin, “Hy girls and boys”. Duk wanda yasan Lulu a family ɗin yasan ba kanwar lasa bace, ba kuma wani take ragawa ba. Duk da mafi yawansu sunada labarin tushen asalin arzikin mahaifin nata da ga kakansune wani bai isa furtawa ba tai masa wankin babban bargo ita babu ruwanta. Yanda tai musu gaisuwar cike da raini ya zafi wasu musamman ma matan amma babu wanda ya nuna, to ita bama ta tsaya sauraren amsawar tasu ba tuni tai gaba, dan a dai-dai nan Alhaji Sufi Garko ke fitowa da ga jirgi gefensa p.a ɗinsa ne da shima zai iya kai sa’annin su Daddy. Lallai ya tsufa kam, damma harka irin ta masu hannu da shuni mai wahalar sha’ani. Amma irin wannan tsoho ai kamata yay ace yana zaune gida jikoki zagaye da shi yana hutawa kawai. Cike da ɗoki da farin cikin murmushi mai bayyana haƙora da ke da tsada a fuskar Lulu dan kafin ka gansa ka yara ta nufi kakan nata ta rungume. Shima tashi fuskar ƙawace da murmushin ya tarbi abarsa yana mai farin ciki da jin kewarta har cikin ransa. Sai da ta gama nata farin cikin sannan sauran yaran suma suka matso garesa su Tajuddeen. Suma ya nuna jin daɗin ganinsu dan yana son ƴan jikokin nasa da a yanzu duk suka zama manya samari da ƴammata har ma da masu aure, dan su Lulu kusan sune ƙanana ma duk da dai suma akwai waɗanda suka girma. Da ga haka aka ɗunguma zuwa gida, inda Lulu ta tubure motarta zai shiga dole kuma akai hakan dan kowa yasan rigimarta original ce. Yanzu kam a hankali take tuƙin dan Alhaji Sufi yayi gargaɗi. Daga shi sai ita ne a motar, dan haka taketa masa hira shiko yan biye mata. Tausayinta yake ji fiye da kowa a cikin zuri’arsa saboda maraicinta, ga kuma ƙaunar da yakema mahaifiyarta itama ya shafeta. A gidan ma koda suka iso sai suka samu ƴaƴansa maza da mata da ke cike da gidan duk dai akan dawowar tasa. A duk sanda akai irin wannan taron da wahala kaga Lulu batai kuka ba koda a ɓoye ne saboda jin buƙatar mahaifiyarta itama. Yanzu ɗin ma da ƙyar take iya danne hawayenta, tama ƙi shiga gidan, tana ganin ƴaƴansa sun janyesa ta zame jikinta ta gudu. Tuƙi take tana hawaye da jin kewa mai tsanani, tasan Mommy uwa ce a gareta, amma da gaske tana buƙatar ɗumin mahaifiyarta koda sau ɗaya ne inda ace hakan zai yuwu, sai dai tasan har gaban abada bazai yiwun ba kuma. Gefen titi ta gangara a hankali ta kashe motar ma baki ɗaya ta lafe cikin kujerar idanunta lumshe tai shiru, so take tai kuka amma tana ƙoƙarin hana kanta hakan. Bata cika son shan komai da rana ba musamman a lokacin aiki, sai dai a yanzu babu abinda tafi buƙata kamar tasha ɗin. Duk yanda taso hana kanta taji shan kawai take buƙata. Cikin rawar jiki ta jawo handbag ɗinta, faudanta ta zaro tare da buɗeta acan ƙasa ta ciro wata takarda da’aka naɗa kamar ƙullin magani. Tana warwareta sai ga ƙwayoyi a ciki. Gaba ɗaya kusan fin biyar duk da ƙananu ne sosai ta afa batare da neman ruwa ba ta haɗe abinta tana wani sauke ajiyar zuciya. (Kamar wadda ta haɗu da uwar tata da take nema😔🤦. Ya rabbi ka shiryemu ka shirya mana zuri’a ka rabamu da mummunar ƙaddara😭🙏)………..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣2️⃣
……..Motar taima key ta cigaba da tafiya duk da ta fara jin kanta ya ɗauka. Da ƙyar ta iya kai kanta office saboda abinda tasha ɗin ya fara aikinsa. A yanda ta shiga duk da bawai tana layi bane yasa mutane da yawa ɗan binta da kallo. Office kawai ta faɗa tare da maidashi ta rufe harda saka key. Tai jifa da handbag ɗinta da key da takalma har ma da mayafi da ɗan kwali. Zama tai jikin kujera ta dunƙule jikinta waje guda tana mai tura kanta data dafe da duka hannu biyu tsakanin ƙafafunta. Surutai takeyi ƙasa-ƙasa irin wanda idan ba kusa da ita kake sosai ba bazaka taɓa iya fahimta ba…
_(Kai jama’a shaye-shaye baiyi ba. Shaye-shaye kan zubar da mutuncinka kowane matsayi ka taka. Yana maidaka baya komai ƙarfin ikon ka. Yana ƙasƙantar da kai komai darajarka. Ga lafiyarka kaima da ɓarnar kuɗi. Miyasa ƴan uwa? Mike birgemu? Mike ruɗarmu?. Kuɗi? Ƙawaye? Abokai? Samari? Gata? Kokuwa son zuciya?. Idan duk sune mu tabbata masu ƙarewa ne kamar ba’ai ba. Masu zama labarine kamar basu zo ba. Shaye-shaye wafce mana dukkan muhimman damammaki yake na cigaban rayuwarmu ta duniya da lahira. Kuduba ku gani, duk shekaru irin na Mawaddat bama tasan minene addininta ba, duk da tarin damammakin rayuwa da ALLAH ya bata wannan illar ɗaya take ta shaye-shaye da ke tare da rayuwarta na ƙoƙarin maidata baya. Tun tana ganin tana kiyayewa akan aikinta gashi ta fara kuma a cikin lokacin aikin, mi kuke tunani? Wataran aikin ma sai ta gagara yinsa gaba ɗaya. Da ga sanda ta rasa wannan damar kuma shike nan ta ƙarasa rushewar baki ɗaya sai jiran ta fara bin bola kuma duk da gatan ta😭. ALLAH ka shiryemu ka shiryar mana da zuri’armu da duk masu wannan mummunar ɗabia)._
★★…..
Bayan sallar la’asar Daddy da Uncle Yousuf suma suka shiga jerin ƴan sannu da zuwa ga Alhaji Sufi Garko. Ya nuna farin cikin ganinsu. Dan mutum ne da ya san mutuntawa. Kallo yake musu suma irin na ƴaƴa tun kan aurattayya ta shiga tsakanin ɗiyarsa da Daddy balle yanzu ga Mawaddat ta ratsa duk da babu ɗiyar tasa data zama sanadi a duniya. A hirarsu ne ma suke jin cewar Mawaddat ce ta ɗakkosa da ga airport, yana ƙyautata zaton ma har yanzu tana a gidan tare da ƴan uwanta. Daddy yaji daɗin hakan har Uncle Yousuf ma kansa. Basu nemeta bata suka cigaba da hirarsu hankali kwance. Shigowar Alhaji Sulaiman (mahaifin Tajuddeen) ce ta saka Daddy yin shiru, sai kuma ya dubi Alh. Sufi Garko da suke kira da Baba cikin girmamawa ya ce, “Baba inaga bara mu wuce ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffara ne”.
Alh. Sufi ya tsatstsare Daddy da idanu batare da ya amsa ba, sai kuma ya maida dubansa ga ɗansa Alh. Sulaiman da ya koma can gefe zai zauna. Cikin bada umarni ya ce, “Isma’il koma ka zauna”. Babu musu Daddy ya koma ya zauna ɗin. Ya maida dubansa ga Alh. Sulaiman da faɗin, “Kaima zonan”. Gaba ɗayansu a gabansa sukaje suka zauna kowa na hararar ɗan uwansa kamar wasu ƙananan yara.
“Ku yanzu kuna ganin wannan rayuwar bazaku ajiyeta ba. Ko a tinaninku har yanzu ku yarane? Ku duba gashin kawunanku furfura duk ta gitta a ciki. Tunda kun gagara faɗamin matsalarku a tsahon shekarun nan ni bazan cigaba da damuwa da sai na sani ba. Sai dai ku sani idan har abinda ya shafeku kuka bari ya shafi zuri’arku bazan yafe ba. Ku shaida hakan ko bayan ƙasa ta rufe idanuna ne”.
(Anzo wajen) cewar Alh. Sulaiman a zuciya. Dan haka ya gyara zama cike da makirci ya sake raunana muryarsa. “Baba ni ba laifina bane, tunda kowa shaidane na biyo hanyar da zamu sasanta da shi a shekarun baya amma ya koma bayan fage ya zuge yarinya komai ya sake rushewa. Shine ya sakama ransa ni maƙiyinsa ne kawai. Shiyyasa naso haɗin auren Tajuddeen da Mawaddat dan ya tabbatar ba hakan bane ba. Kuma ko a yanzu in har zai amince ya cire komai a ransa ni a shirye nake komai ya zama labari. Mu kuma dunƙule ƴaƴanmu waje guda matsayin ma’aurata dan ƙara danƙon zumincinmu”.
Wani irin kallon ɓacin rai Daddy ke masa. Sai dai baice komai ba. Alh. Sulaiman da ke masa kallon ƙasa-ƙasa ya saki wani irin makirin murmushi da kashe masa ido ɗaya. Ƙara tunzura zuciyar Daddy tai amma sai ya danne dan jin Baba ya fara faɗin, “Ni kaina zanso wannan haɗin zumincin, zan kuma so ya zama sanadin canja wannan gabar taku. Sai dai kuma bazan so ya rikiɗe daga manufarmu ya koma abinda bashi muke fata ba zumincin ya taɓarɓare ma fiye da yanzu….”
“Amma Baba ai yaran suna matuƙar son junansu. Dama tun farko matsalarmu ce ta tilastasu haƙura a wancan karon ma”. Alh. Sulaiman ya faɗa yana sake sakin makirin murmushi. Baba da ba ganin abinda ke faruwa yake ba ya kai dubansa ga Daddy da baice komai ba. “Isma’il bakace komai ba. Abinda ɗan uwanka ke faɗa gaskiya ne?”.
Murmushin mugunta Daddy dake ƙulla murtanin da zai maida ga Alh. Sulaiman ya saki. Cike da sake girmamawa ga surukin nasa kuma ogansa ya jinjina kansa. “Baba duk ina saurarensa. Sai dai na tafi wani tunani ne, kenan Mawaddat ƙarya tamun ko kuwa rashin jin nata ne ya sata kawo min wani a matsayin miji alhalin suna tare da Tajuddeen har yanzu…”
“Miji?”.
Alh. Sulaiman ya faɗa kamar a ɗan razane. Shiko Baba murmushi yayi da faɗin “Miji Mawaddat ɗin ta fitar?”.
“Eh Baba. Dan dama dawowarka muke zaman jira muzo maka da batun. Saboda yanata ma damuwar turo magabatansa amma ina dakatarwa da cewar har sai ka dawo tukunna”.
“Wlhy ƙarya kake Isma’il! Wannan makirci ne ka ƙulla dan kar Mawaddat ta auri Tajuddeen, an gaya maka tsoronka nakeji wai ne da na gagara ɗaukar mataki a kanka tun a baya”. Alh. Sulaiman ya faɗa yana miƙewa zumbur. Gaba ɗaya falon suka zuba masa ido. Sai kuma duk ya daburce dan fahimtar yana neman yin ɓaran ɓarama fa.
“Ka ɗauki mataki a kansa! A wane dalili Sulaiman?”. Baba ya katse shirun. Kame-kame Alh. Sulaiman ya fara, hakan ya bama Daddy damar sakin murmushin mugunta. Sai kuma ya dubi Baba. “Baba ƙyalesa kawai shirmensa ne. Kasan shi Sulaiman idan ya fusata akan abu baida fahimta. Sannan ya iya sakin duk maganar da tazo masa a baki koda ba hakan bane a ransa. Ni dai ba ƙin haɗin auren Mawaddat da Tajuddeen nake ba. Kawai shashancin da tayi ne na kawo min wani matsayin miji da har na sanar da nawa dangin dama jiranka kawai muke ka dawo a tsaida biki alhalin tana tare da Tajuddeen kuma ne yasa ma harna faɗa. Amma ayi haƙuri ni zanje ga babanta Yousuf mu sameta a nutse na mata tambayoyi dan nasan halinta bajin magana take ba. Kaga idan Tajuddeen take so ni bazan hana ba, sai nasan dabarar yi wancan ya janye a rabu lafiya mutuncin kowa bai zube ba….”
“Mizai hana w kirata yanzu ayita ta ƙare”.
Cewar Alh. Sulaiman. Shiru kamar Baba bazaice komai ba. Sai kuma ya nisa a hankali da faɗin, “Ku dukanku kunzo da shawara mai ƙyau kuma duk na gamsu da maganarku. Sai dai muyi haƙurin goben sai a zauna a nutse kan maganar. Amma yanzu ina son a kiramin Mawaddat da Tajuddeen”.
Sosai hankalin Daddy ya tashi, amma ya danne a ransa yana mai addu’ar ALLAH yasa kada Mawaddat ta watsa masa ƙasa a ido. Dan shifa bazai taɓa yarda ya haɗa zuri’a da Sulaiman ba. Shi kansa Uncle Yousuf zancen Yayan nasa ya sakashi a ruɗani. Duk da yasan akwai ƴar tsamar da har yanzu bai san tushen ta ba tsakanin ɗan uwan nasa da Alh. Sulaiman bai san dalilinsa na ambaton wani ba matsayin Mawaddat ta kawo bayan yasan ba hakan bane ba. Kusan a tare suka saki ajiyar zuciya shi da Daddy lokacin da ɗan aiken ya dawo ya tabbatar musu ai Mawaddat ance ta tafi tunma ɗazun. Alh. Sulaiman kuwa bai so haka ba. Amma baice komai ba, sai dai a ransa yana ƙudurta duk Daddy yayi ya gama a wannan karon sai Mawaddat ta zama matar Tajuddeen…..
😂Anayi muna cin tuwon masara miyar kuka🤪.
★★..★★
Yau gaba ɗaya a gida ya yini saboda tun daren jiya Uncle Yousuf ya ce masa karfa ya fito aiki yau ɗin ya bari har sai yaji ƙarfin jikinsa. Hakan ya saka shi yin zamansa tunda dama sunyi faɗa da ogar tasa. Ɓoye kansa yay a ɗaki ya sha barci, hakan yasa babu wanda yasan yana gidan ballema ya tuhumesa tunda bai sanar musu abinda ya samesa ba. Bayan sallar la’asar gaba ɗaya kuma sai zaman gidan ya gunduresa. Hakan ya sashi miƙewa ya kimtsa. Yayi ƙyau cikin ƙanan kayan duk da shi bawai ya saka don kwalliya bane ba. Ƙamshin turarensa yake mai sanyi da sakama zuciya nutsuwa. Sai da ya fito ya fara tunanin inama ya dace ya nufa? Duk da har yanzu yana jin jikinsa babu kuzari sosai. Rashin mafitar ina ya kamata ya nufa ya sashi kallon agogo, yasan yanzu bata tashi aiki ba, bara ya gwada zuwa idan ta huce sai ya maidata gida kawai, yafi ya tafi yawo mara dalili. Napep ya tare ya shiga.
Zuwa yanzu gaba ɗaya yanayinta ya sake birkucewa, ta zame ribbon ɗin data ɗaure dogon gashinta da ya sauka har kafaɗarta. Sosai idanunta sunyi jazur haɗe da kumburowa. Surutai take ita kaɗai da gaba ɗayansu na bege ne ga mahaifiyarta. Sai kuma zagin mijin matar nan da yay fyaɗe tare da ɗaukawa kanta alƙawarin koya masa hankali da duk ire-irensa. Hawaye take da murmushi a lokaci ɗaya, yayinda ta ƙurama hoton mahaifiyarta da ta ɗakko saman decks ɗinta dake a cikin wani ɗan ƙyaƙyƙyawan fram ita da Daddynta, hoton anyisa ne bayan aurensu a ƙasar Mexico lokacin sunje honeymoon. Su dukansu suna sanye ne a cikin ƙanan kaya suna kallon juna da murmushi mai nuna tsantsar soyayya da sukema juna. Hannunta ta kai ta shafa fuskokinsu, sai kuma ta rungume hoton tana mai komawa kwance rigingine ta ƙurama p.o.p ɗin office ɗin ido. Ƙwayar tata ce ta fara gaya mata shirme ga mahaifiyarta a wajen cikin farin tufafi tana mata kallo mai kama da tausayi………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣3️⃣
…….Bai san ainahin Office ɗin nata ba, sai dai ganin motarta a harabar wajen ya sake tabbatar masa da tananan bata wuce ba. Tunanin zaman jiran fitowarta yayi, hakan ya sashi samun wajen zama a gurin securitys. Bayan gaisuwa a tsakaninsu bai sake kula kowa ba ya shiga sana’ar tasa ta game ɗin ball a waya. Biyar dai-dai babu alamar zata fito, tun yana ɗan ɗagowa ko zai hangota har ya fara sarewa ganin biyar da rabi har ta gota ma. Ga mafi yawan ma’aikata sun wuce dan motarta da wasu biyu ne kawai suka rage a harabar wajen. Ɗaya da ga cikin security ɗin ne ya dubesa tare da faɗin, “Abokina wanda kake jira har yanzu bai ƙaraso bane? Dan shida dai-dai ake rufe wajen nan fa”.
Wayar ya ajiye tare da ɗagowa ya dubi security ɗin fuskarsa a ɗan sake, sai dai ba murmushi yake ba. “Wadda nake jira tana ciki dan ga motarta nan, nima ina tunanin ko lafiya har iyanzu bata fito ba”.
“Kana nufin Madam Mawaddat Jiƙamshi?”.
Kai ya jinjina masa alamar ita. Shima security ɗin cikin nuna jimami ya ce, “Inaga dai yau aiki ne yay mata yawa gaskiya, dan a kullum zakaga idan bata zama ta farkon tashi ba to zata zama ta biyu. Nima kaina nayi mamakin rashin fitowar tata yau duk da dai naga wani aiki tasa a gaba kwana biyun nan mai muhimmanci. Amma bari na duba maka maybe bata san kana zaman jiranta bane”.
Kafin Smart ya samu damar cewa wani abu security ɗin yay gaba. Minti kusan uku sai gashi ya dawo. “Abokina inagafa kamar akwai matsala”.
“Matsala kuma? Tami fa?”. Smart ya faɗa ƙirjinsa na bugawa da sauri-sauri. Amma sai ya dake abinsa kamar babu komai. Security ɗin ya cigaba da faɗin, “Bawai matsalar bace a zahirance, na samu sakatariyarta ce kawai zaune cikin damuwar wai tun ɗazun data fita ta dawo ta shige office ta rufe kanta har yanzu bata fito ba. Ta mata knocking kuma yafi sau ashirin batako ji motsinta ba sai yanzu babu jimawa taji maganarta kamar cikin surutai”.
Ƙirjinsa ne yaji ya ƙara bugawa, ya kai yatsunsa biyu saman goshi ya ɗan murza. Basai ya nema ƙarin bayani ba yasan wani abu tasha. Sai dai bai taɓa tunanin har a wajen aikinta ma tana shan abubuwan nan ba. Ɗagowa yay idanunsa har sun kaɗa da ɓacin rai. “Kozan iya shiga office ɗin nata?”. Ya tambayi security ɗin.
“Ah eh mana mizai hana. Ai gara a je a duba mike faruwa ko?”.
Miƙewa kawai yay, security ɗin yay masa jagora har office ɗin. Sun samu sakatariyarta tsaye jikin ƙofar tana knocking da faman kiran “Aunty! Aunty Please ki buɗe ko kiyi magana dan ALLAH.”
“Kinga ƙyaleta idan da key bani”. Ya faɗa cikin dakewa. Cikar kamala da kwarjininsa yasa Zainab jin bazata iya musa masa ba. Duk da kuwa yau ne karo na farko data taɓa ganinsa anan ɗin. Sai kuma ganin harda security ya ƙara mata ƙarfin gwiwa. Muryarta a sanyaye ta ce, “Sai dai na duba ko zanga extra keys dan ta shiga da key ɗin ciki”. Kansa kawai ya jinjina mata, ta koma wajen table ɗinta domin bincikawa. Shi kuma ya jingina da bango tare da harɗe hannayensa a ƙirji ya lumshe idanunsa. Kusan mintina huɗu tana ta binci-bincike har dai ta samo keys ɗin da ƙyar. Gabansa tazo ta miƙa masa cikin girmamawa.
“Thanks” yace a hankali yana amsa. Koda ya buɗe ƙofar bai yarda ita da security ɗin sun biyosa ba sai da ya leƙa. Saurin rumtse idanunsa yay tare da yo baya, cikin ɗan furzar da huci ya gyara yanayin fuskarsa yanda zasu fahimcesa. “Inaga bata da lafiya ne, kun san halin ogar taku kuma maybe bata buƙatar kowa ya sani shiyyasa taya rufe kanta a ciki, ku barni da ita kar ku samu rabon faɗa kuma”. A yanda yay maganar dole ne ka gamsu, dan haka security ɗin yay murmushi dan kuwa masifar Mawaddat kowa ya santa, idan sukai sanya wajen buɗe mata gate kota saka wani aikin kai mata wasa sai ta tsefeka tas. Balle ma Zainab da tafi kowa sanin wacece uwargijiyar tata. Sallama security yay ya fita, Zainab kuma ta koma mazauninta ta zauna duk da ya kamata ace ta tashi, amma dai tafi yarda taga sai Mawaddat ta fito lafiya sannan. Ƙofar ya sake turawa ya shiga ya maida ya rufe tare da jingina jikinta kansa a ƙasa bai yarda ya sake kalloba. Kamata yay ya kira Zainab, sai dai baya son ta ganta a yanayin. Har yanzu tana kwance a tsakkiyar sofas ɗin da aka shirya dan zama bayan ta zamanta da wanda ke a gaban table ɗin nata. Ta ture Centre table ɗin tsakkiyar kujerun tana kan carpet ɗin gashinta yaɗan barbaje. Har yanzu idanunta na kallon p.o.p ɗin office ɗin, hira take da mamanta da idanunta ke gani ko nace ƙwaya take siffanta mata. Hawaye share-share a fuskarta ga murmushi. Tsaiwarsa gurin shiru na wasu sakanni ya sashi ɗan jin soki burutsunta. A karo na farko ya ɗaga kansa ya dubi p.o.p ɗin shima jin tana faɗin, “Mammah karki sake tafiya ki barni kinji. Kiyi zamanki muyi hirarmu, inma bazaki min magana ba ni zan na miki murmushinki ya wadatar dani. Kar kiyi kuka a kaina bana son ganin hawayenki ki bari Please ki bari…” ta faɗa cikin wani irin sanyin murya sai kuma ta fashe da kuka. Da farko bai ɗauki surutun nata komai ba sai shirme irin na masu shaye-shaye, sai dai Mammah da take ambata ya tsaya masa a zuciya. Ganin yana ɓata lokaci ya sashi furzar da ƙaramin iska tare da cigaba da takawa cikin office ɗin, ƴan dube-dube yake yi duk da baiyi tsammanin zai iya dacewa da abinda yake neman ba. Dama baiyi tsammanin ganin ba ai. Fita yay inda sakatariyarta ta take, tana zaune dai har yanzu sai dai yanzu da waya a hannunta, dan tunda ta turama Uncle Yousuf text take tsammanin shigowar kiransa amma shiru kake ji.
“Ko zamu samu Hijjab?”.
Firgigit ta dawo a hayyacinta dan jin saukar deep voice ɗin sa a bazata cikin kunnen ta. Sake maimaita mata yay ganin kamar bata jisa ba. Kanta ta gyaɗa masa da sauri tana nufar inda ta jiye hijjab ɗin sallarta ta ɗakko masa. Amsa yay kawai ya koma ciki. Yana ɗan sauke ajiyar zuciya, yanzun ma bai yarda ya kalletan ba ya warware hijjab ɗin tare da kaiwa duƙe gabanta. Karan farko na rayuwarsa ya ambaci “Mawaddat!” cikin ɗacin murya da tausasawa, sai dai acan ƙasan makoshinsa zaka iya fahimtar jin zafinta. Ƙarfin muryarsa da yanda yay kiran nata ya saka shigar sautin cikin kunnenta a bazata. Kamar wadda aka farkar a cikin barci ta juyo idanunta da suka sake girma da ɗan juyewa kansa. “What!” ta faɗa a zabure tana tashi zaune sosai. Sai kuma ta kalla sama da ɗaga hanunta. “Mammah ki jirani dan ALLAH”.
Kallonta yay jin abinda ta sake faɗa, hakan sai yay dai-dai da yanda ta zuba masa juyayyun idanunta fuska a yatsine tana wani ƙwaɓeta ta ce, “Who are you? Miya kawo ka nan?”.
Tsaki ya saki tare da ɗauke idanunsa ya yafa mata hijjab ɗin a jiki. Hannun da takai cikin yar kokawar ture hijjab ɗin ya buge. Da sauri ta janye tare da faɗin “ouch!” saboda zafin da taji. Baibi takanta ba ya ƙarasa saka mata hijjab ɗin batare da ya yarda ya taɓa mata jiki ba. Wata muguwar harara ta watsa masa ta ƙara kai hannu zata cire hijjab ɗin ya daka mata tsawa.
“Idan kika cireshi na rantse sai na canja ma fuskarki kammani da mari!!”
Sosai tsawar tasa ta ratsata. Gaba ɗaya sai ya sake juye mata a cikin idanu kamar wani bahagon zaki. Kuka ta saki da duban p.o.p ɗin ta ce, “Mammah kinga yana min ihu ko. Bana son shi yanada girman kai”.
Bakinsa kawai ya taɓe da cigaba da tattare kayayyakinta data barbaza a office ɗin waje guda, a zuciyarsa yana faɗin (aike naki kan ƙarami ne). A dai-dai nan aka turo ƙofar aka shigo. Juyowa yay da ɗan sauri dan a tunaninsa sakatariyarta ce, amma sai ya ga Uncle Yousuf ne. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke dan gaskiya yaji daɗin zuwan nasa. Dama sai faman ƙullawa da kwancewar ta yanda zai fita da ita a office ɗin yake. “Barka da yamma Alhaji”.
Murmushin ƙarfin hali Uncle Yousuf ya saki yana jinjina kasa, sai kuma ya maida dubansa ga Lulu da har yanzu ke sambatunta irin na rashin kasancewa a hayyaci. Idanu ya ƙura mata da kamar wanda ya zurfafa kansa a tunani, maganar Smart ta sakashi yin firgigit. Cikin ƙoƙarin shanye abu mai ƙona zuciya ya sake dubansa da murmushi. “Aliyu ya jikin naka? Kai da nace yau karkazo aiki shine kuma ka fito?”.
“Naji sauƙi ai Alhaji. Kasan zaman gidan isar mutum yake yi shiyyasa na fito. Nafito ɗin kuma na rasa ina zan nufa shine kawai nace Bara na duba ko bata tashi aiki ba sai na maidata..”
Uncle Yousuf da ke jin zuciyarsa babu daɗi ya kai zaune yana mai tallafo haɓarsa. Kusa da shi ya nunama Smart da ke kallonsa. Babu musu ya zauna sai dai a kujerar gefensa. Ya fahimci irin damuwar da Uncle Yousuf ɗin ya shiga, dan haka sai shi ya ɗan sassauta tasa cikin furzar da ƙaramin huci. “Alhaji damuwa bata zama maganin matsala ba, sai dai ta zama sanadin ƙirƙirar sabuwar matsala wa rayuwa…..”
“Hakane Aliyu. Amma ka duba fa kenan har a wajen aikinta ma tana sha? Hakan kuma na nufin duniya ta jima da sanin halin da Mawaddat ke a ciki amma mu bamu sani ba”.
“Banajin hakan gaskiya Alhaji”.
Idanu kawai Uncle Yousuf ya tsira masa, dan haka office ɗin yay shiru sai surutan Lulu kawai ke tashi cikin sambatun maye. Kiran da ya shigo a wayar Uncle Yousuf ɗin ce ta katse shirun nasu. Kamar zai share sai kuma dai ya cirota a aljihu. Daddy ne, yasan jiransa ya keyi dan sun zauna zasuyi magana ne Zainab ta tura masa saƙo shine ya taho hankali tashe. Wayar ya ɗaga tare da kaiwa kunnensa. Muryarsa a sanyaye ya ce, “Yaya!”.
Daddy da tun fitowar ƙanin nasa ya kasa zaune ya kasa tsaye ya ce, “Yousef miya faru da ita?”.
“Babu komai yaya ka kwantar da hankalinka dan ALLAH. Dan nama tadda Aliyu har yazo ma shi….”
“Waye Aliyu? Ko drivern ta?”.
“Eh yaya.”
“Ka faɗa min gaskiya Yousuf abubuwan tasha ko?”.
“Yaya dan ALLAH k…”
“Yousef please”.
Daddy ya faɗa cikin tare numfashin Uncle Yousuf ɗin. Cikin sakin ajiyar zuciya ya ce, “Hakane. Amma dan ALLAH ka kwantar da hankalinka, gamu nan tahowa gidan ma”. Daga haka ya yanke wayar. Shi ya ɗauki Lulu kamar ranar, Smart kuma ya fita da kayayyakinta a hannu. Zainab da gaba ɗaya hankalinta ya tashi da ganin yanda aka fiddo auntyn tata ya kalla. “Ki rufe office ɗin ki sameni waje a maidaki gida”. Daga haka yay ficewarsa.
Kamar yanda ya bata umarni hakan tayi, lokacin data fito har Uncle Yousuf da ya saka Mawaddat a motarsa yana ƙoƙarin ficewa a gidan. Yayinda smart ke tsaye yana jiranta. Batare da yi mata magana ba ya shiga motar, itama sai ta buɗe ta shiga kusa da shi. Har gida ya kaita abisa kwatancen da tai masa, godiya taita masa cikin girmamawa, karan farko yay mata guntun murmushi cikin jinjina kai ya ja motar ya wuce……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣4️⃣
…….Idanu kawai Daddy ya zubama Mawaddat hawaye na kwaranya saman dattijuwar fuskarsa. Itako sai surutai take musu. Sai ta kalla Daddy tayi ta kalla Uncle Yousuf shima tayi. “Yaya kukan nan fa bashi da wata ma’ana, addu’a itace kawai. Sannan bazan gaji da faɗa makaba ka bada kaso mafi yawa akan shiga wannan yanayin nata. Sai dai kawai muyi ƙoƙarin gyara kuskuren a yanzu. Ga kuma wannan matsalar data kutso kai, duk da dai ni da za’a bi ta tawa da kawai a aura ma Tajuddeen ɗin tunda mun san dai yaron nan bashi da wani aibu a rayuwarsa…..”
“Yousuf matsalar ba daga Tajuddeen take ba da ga mahaifinsa ne. Nasan abinda baka sani ba akan sulaiman sani na haƙiƙa. Kamar yanda na faɗa maka tun a wancan karon Tajuddeen an kwaɗaita masa son Mawaddat ne kawai da manufa, sai dai shi yaron ya afka batare da sanin manufar mahaifin nasa ba, ko kuma dama yana son nata shiyyasa Sulaiman yay amfani da wannan damar wajen sake jan zuciyarsa da tunanin hakan zai bashi nasara akaina.”
“To amma yaya ai shine zai zauna da ita ba Mahaifinsa ba. Indai har mun tabbatar da yana son nata kamar haka banga aibun aura masa ita ba. Na sani ka sani Mawaddat bata kula kowa, ta ina shi mijin daka ambata gaban Baba zamu samar da shi? Dan kasan dai in har babu wannan mijin to dolene Mawaddat ta auri Tajuddeen tunda baba da dangin mahaifiyarta duka sun ɗauki abin da muhimmanci bakuma zasu taɓa bijirema umarnin mahaifinsu ba kamar yanda suka saba”.
“Duk nasan da wannan Yousuf. Kuma nima damuwata a yanzu shine ta yanda zamu samar da mijin koda ace na wucin gadi ne kafin ƙura ta lafa.”
“Wucin gadi kuma?”.
“Yes wucin gadi, dan ba zan taɓa yima yaranmu ko ɗaya auren dole ba. Auren ma da jini irin na Sulaiman mai shirye da manufofi masu yawa da sai anyi auren ne sun fara bayyana zaka fara dana sani kai kanka”.
Shiru kawai Uncle Yousuf yay yana kallonsa, shi kam gaba ɗaya ma a wannan gaɓar ya shiga ruɗani zai ce. Ya kasa fahimtar ainahin abinda ke tsakanin yayan nasa da yayan matarsa da a shekarun baya suka kasance shaƙiƙan abokai da ko ƙuda baya iya jin sirrinsu. Anya kuwa yayansa baya ɓoye masa wani babban al’amari da ya kamata ace ya sani…..
“Assalamu alaikum”. Sallamar Smart a ƙofar falon ta katse tunaninsa. Daddy ne ya amsa tare da bada izinin shigowa dan ya shaida muryar yaron. Akan Lulu da ke kwance a ƙasa barci na neman rinjayar idanunta tana kokawar hanashi ya fara sauke idanunsa. Kaudasu yay duk da sanye take da hijjab ɗin da ya saka mata har yanzun. A nutsensa ya gaishe da Daddy, tare da ajiye key ɗin motar hannunsa. “Sannu da ƙoƙari fa, ALLAH ya saka maka da alkairi kaji”. Daddy ya faɗa a karo na farko. Ɗan murmushi Smart yay cikin jinjina kai. “Babu damuwa ai Alhaji. Nima na gode. Bara na wuce gida”.
Godiya Daddyn ya sake masa, tare da zaro kuɗaɗe masu yawa da ga aljihunsa ya miƙa masa. Kallon kuɗin Smart yay da sake sakin murmushi mai ma’anoni da yawa sai kuma ya girgiza kansa. “A’a Alhaji nagode sosai. Amma bazan amsa ba, albashin da ake biyana ya wadatar dani ALLAH ya ƙara buɗi”. Mamaki matuƙa Daddy ya shiga, dan haka ya kalla Uncle Yousuf da tun shigowar Smart ɗin baice komai ba. Kafaɗa ya ɗage masa alamar haka yake. Ai Daddy kasa ƙara cewa komai ma yayi har Smart ya sake musu sallama ya fice abinsa…..
★★ *_8:25pm_* ★★
Ƙarfe takwas da kusan rabi na dare tawagar Hon. Babale Nakowa da su Alhaji Baita suka isa gidan Alhaji Sufi Ado Garko kamar yanda suka tsara. Ziyara ce ta bazata, dan haka Alh. Sufi yay mamakin zuwan nasu duk da kuwa su dukansu sun kasance yaransa ne ta fannoni daban-daban kafin yau. Sai dai duk da kasancewar wannan zuwa nasu ya kasance na bazatan hakan bai hana su sami tarba ta mutuntawa ba. Bayan sun gaisa da Alh. Sufi cikin girmamawa a matsayinsa na _God Father_ nasu sai kuma hira ta ɓalle mafi ƙarfi akan kasuwanci da siyasa. Sun ɗan taɓa hira kafin Hon. Misau ya fara bayani akan abinda ya kawosu.
“Ranka ya daɗe mufa zuwan nan namu kamar gaisuwa ce da roƙon iri. Munzo mu maka Barka da dawowa da kuma yaya jiki sai kuma babbar magana mai alaƙa da son ƙulla sabon zumincin da muka san kaima zakayi farin ciki da shi”.
Cikin mamaki da dattijantaka Baba yay murmushinsu na manya idonsa akan Alhaji Misau. “Jeka maganarka kai tsaye Ɗan kande! kasan ni a koda yaushe nafi buƙatar abu abuɗe fiye da rufa-rufa”.
“Hakane Baba”.
Cewar Hon.. Misau cikin murmushi da sake gyara zama. Sai da ya ƙara juya zancen a ransa ta yanda zai fito da armashi sannan ya cigaba da faɗin, “Akwai wata yarinya a cikin zuri’arka da Alhaji Haruna ya gani ya kuma ji ta kwanta masa matuƙa a rai saboda nutsuwarta da hankalinta. Da farko mun shirya tunkarar mahaifinta sai kuma mukai tunanin ai baba ma da babansa. Shiyyasa muka dakata har sai yau daka dawo mukazo da ɗumi-ɗumi dan a tabbatar bada wasa muke ba”.
Murmushin mai cike da jin daɗi Alhaji Sufi Garko ya saki tare da faɗin, “Kai kai Masha ALLAH. Masha ALLAH, naji daɗin hakan kuma zanayi matuƙar farin ciki saboda sani da naima Haruna a rayuwa da nagartarsa. Amma wace yarinya ce wanna haka?”.
Yanzu kama Hon. Baita ne ya nisa shima da murmushin shinshino nasara akan fuskarsa ya ce, “Baba sunanta Mawaddat. Ƴar wajen Alhaji Isma’il Jiƙamshi. Kaga a gareku ku jikace.”
“To to! Ko kaine dama yake faɗa mijin data fidda ɗin? Dan ɗazun dama muke magana akan ɗan wajen Sulaiman da aka taɓa son haɗa su sai abin bai yiwu ba da yake a lokacin ba matarsa bace.”
Kallon juna sukai kowanne zuciyarsa kamar zata ɓallo ƙirji ta fito, sai kuma suka haɗa baki wajen faɗin, “Aiko bazai wuce hakan ba kam”.
Duk da maganar ta ɗan yima Alhaji Sufi Garko gingirin a zuciya sai kuma hakan bai hanashi jin daɗi ba da nuna farin cikin sa. Dan haka babu wani kwalo-kwalo ko jan magana ya tabbatar musu suje gida insha ALLAHU zuwa gobe su dawo garesa da shirinsu bayan sallar azhar zasu samu amsa mai gamsarwa. Dan ya tabbatar musu duk da shi kaka ne ta ɓangaren mahaifiya yana da nasa ƙarfin ta wani fanin ma ubane shi ga mahaifin nata shima ai. Farin ciki iya farin ciki sun shiga, dan haka suka tafi da ƙwarin gwiwar samun nasara batare da sun sha wata wahala ba. Gefe ɗaya kuma suna dariyar muguntar kama Daddy a tafin hannunsa ta inda bai zato ba ko tsammani. Ko a mota hirar da suka dinga yi kenan cike da jin alfahari…..
★★ ……
Tun bayan wucewar Uncle Yousuf da ya maida Mawaddat ɗakinta batare da ko ɗaya a cikin ƙannenta ya ganta ba shima ya shige nasa ɗakin ya kulle kansa dan samun damar yin isasshen tunani. Ƙarar wayarsa ce ta katse masa dogon lissafin da zuciyarsa tai nisa a yi. Jawota yay cikin jan ƙaramin tsaki zai kashe yaci karo da sunan _Baba garko._ Tashi yay zaune sosai, sai dai bai ɗaga ba har sai da ta yanke shi yay kiransa. Dan haka dama yake masa. Cikin girmamawa ya gaida ogan nasa kuma surukinsa. Da kulawa Baba ya amsa. Ta re da faɗin, “Isma’il ko ka fara barci ne na tasheka amin afuwa. Na kasa haɗiye abin farin cikin nan ne shiyyasa na nemeka yanzu ɗin. Ashe baƙon da kake maganar ɗazun na gida ne…..”
“Baba baƙo kuma?”.
“Eh baƙo mana Isma’il. Mai auren Mawaddat mana. Dan yanzu nan suka wuce su sarakan zumuɗin ma sun kasa haƙuri har sun kawo kansu. Ko kuma ja’irar ƴar taka ce ta turosu ma dan kasanta da gaggawa”.
Sosai ƙirjin Daddy ke lugude. Duk da shi sam yama kasa fahimtar Baba ɗin yanda ya kamata. Kasa jurewa yay dai yace, “Baba kai min afuwa. Wlhy ban gane akan wa kake magana ba. Dan inada tabbacin Mawaddat bata turo kowa ba kasancewar ma ni bamu zauna magana ba dan na sameta kwance a gida ma kanta na ciwo tun bayan ɗakkoka airport”.
“Tofa wata sabuwa kenan? Su Alhaji Baita ne fa suka sameni a daren nan kan wai Hon. Haruna Dauda Nakowa na son Mawaddat har ma sun dai-daita kansu kaima kuma kasan maganar ma. A yanzu haka ma na basu damar dawowa a gobe idan ALLAH ya kaimu da shirins…..”
Cikin suɓutar baki Daddy ya furta, “What! Su Alh. Ɗan-kande Baita fa kace baba?”.
“Eh ƙwarai su ɗin fa na faɗa Isma’il. Shin akwai matsala ne?”.
Yawune ya nema sarƙe Daddy, da ƙyar ya iya figo glass cup ɗin ruwa dake a bed side drawer ya kwankwaɗa. “Baba ni wlhy bamma san akwai wata alaƙa tsakanin Mawaddat da su Alhaji Baita ba sam. Sannan kuma bana jin ita ɗince ma ta turosu. Dan yaron da take so ɗin wanine daban”.
“Ikon ALLAH to mi hakan ke nufi?”. Cewar baba. Daddy da takaici da damuwa suka lulluɓe a lokaci guda ya ce, “Baba wlhy ban san manufa ko dalilinsu nayin duk hakan ba. Danni nasan Mawaddat bata da wani alaƙa da su”.
“Uhhmm to kaga ina ganin mu ajiye maganar nan to. Amma ka tabbatar gobe idan ALLAH ya kaimu a wajen taruwar meeting ɗin nan kazo min da Mawaddat, idan ma zai yiwu harda shi wanda take so ɗin”.
Godiya Daddy yay masa. Yayinda tuni yay jagaf da zufa. Kamar wanda ya fito a wanka. Gaba ɗaya lissafinsa ya rushe shi yanzu ma baya gane komai ma. Wayar ya ɗauka yay kiran Uncle Yousuf. Ba’a ɗaga ba sai da tai gab da tsinkewa. Ko sauraren tambayar da Uncle Yousuf ɗin ke masa bai yiba. Sai ma katsesa yay da faɗin, “Yousef akwai matsala. Tabbas akwai matsala. Amma ka jirani ina zuwa gidanka ɗin yanzu”.
“Haba-haba yaya da kanka. Inaga ka jirani kawai gani nan zuwa”.
“Karka damu Yousuf kai dai ka jirani kawai. Nan ɗin zaifi sirri ”.
Babu yanda Uncle Yousuf ya iya dole yabi umarnin nashi yay zaman jiransa. Mintinan da basu wace goma sha ba sai ga Daddy ya iso……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣5️⃣
…….A harabar gidan ya sami Uncle Yousuf ɗin tsaye da alama shi yake jira shima. Ciki suka shiga har falonsa. Tsaf daddy ya kwashe ya sanar masa da duk abinda surukinsa kuma ogansa ya kira shi yanzu nan. Karan farko shima Uncle Yousuf ya girgiza. Duk da sam bai gane ainahin manufar shiga Daddy a ruɗani ba. Kwantar masa da hankali Uncle Yousuf ya shiga ƙoƙarin yi, amma sai Daddy ya dakatar da faɗin, “Yousuf bamu da wani lokaci isashe. Minene mafita. Dan wlhy wlhy kaji na rantse maka. Suma da wata manufa sukaje ga baba, kuma lallai dole akwai wata a ƙasa …”
“A ƙasa kamar ya?. Nifa yaya ƙara dilmiyar dani kake wlhy akan al’amarin nan, sannan ka fara bani tsoro. Dan ALLAH ka bani abuɗe mana ko zanfi sanin makamar riƙewa ta ƙwarai”.
“Zan baka amma ba yanzu ba Yousuf. Yanzu hanyar kuɓutar da Mawaddat da mu kammu gaba ɗaya kawai ya kamata mu nema dan ALLAH. Idan ba haka ba komai zai canja da ga yanda muka sanshi zuwa a yanda bamuyi zato ko tsammaninsa ba. Miye mafita? Wa zamu kai matsayin miji ga Mawaddat? Dan fa dole ne mu samar da wannan mijin saboda Baba baya magana biyu. Sannan duk waɗan nan mutanen suna da tasirin da zai iya zartar da hukuncin basu Mawaddat ko ina so ko bana so musamman akan abinda ya faru a baya da kuma gargaɗi da sharaɗin daya shimfiɗa mata kan duk wanda yazo neman aurenta zai bashi kota yarda ko bata yarda ba”.
“Hakane yaya, sai dai yanzu mu a ina zamu iya samo miji? Sai nake ga ya kamata itama Mawaddat ɗin mu tuntuɓeta ko?”.
“Tuntuɓar tata yana da amfani, sai dai kuma zuciyata na raya min wani abu. Mizai hana mu jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya ne”.
“Okay yaya kamar ya kenan?”.
“Yauwa abinda nake nufi anan itama mu barta a rufen kawai mu samar da mijin amma na bogi dan fatana kawai mu nunasa ga Baba dan abar zancen, ita kuma mu nuna mata hukuncinta kenan akan wannan halayyar tata, sai ta gama wajiguwa matuƙa sannan mu faɗa mata gaskiya mu kuma bata damar fidda mijin da take so. Amma yaya ka gani kai?”.
Uncle Yousuf da shima ya gama tsara nasa tunanin tun fara maganar yayan nasa yay wani shegen murmushi da faɗin, “Tabbas hakan yayi, kuma ina ganin mutum ɗaya ne zai iya mana wannan aikin, sai dai maganar riƙe hakan matsayin hukunci gareta ko barazana bazai taɓa canja abinda muke fatan canjuwarsa ba da ga gareta. A halin da Mawaddat ke ciki canjata na nufin bin wasu matakai daki-daki dan tayi nisan da ƙyamatar ta ko mata hargagi bazai kasance hanyar gyarata ba”.
“Na yarda da kai auta, shiyyasa akoda yaushe nake kasancewa a farin ciki da ƙwarin gwiwa idan kana a kusa da ni. Amma wanene shi ɗin?”.
“Aliyu drivern ta Yaya”.
Da sauri Daddy ya ce, “Haba Yousuf driver fa? Ina mudai samar da wani mai darajar da tafi tashi ko cikin yaran abokaina haka ko a cikin ma abokanka”.
“Yaya kenan, amma karka manta fa cewa dai ba auren za’ai ba. Zamu samar da mijin ne kawai dan ai mata kurari sannan mu toshe waccan damuwar da aka kasa a teburin Baba. To indai hakane ai kuwa shi wannan da kake ganin bai kai ba ne dai-dai da wannan shirin namu. Amma waɗan can zasu iya zamar mana ƙarfen ƙafa, shi kaɗai ne makamin da zamu riƙe, inada yaƙinin zai taimake mu wajen yakin nan har muci nasara”.
“Eh kuma fa haka ne gaskiya Yousuf na fahimceka kuma. Yanzu minene mafita?”.
“Karka damu bar komai a hannuna. Kai dai ka zama cikin shiri kawai itama Mawaddat ɗin ka barni da ita, ka koma kawai gefe ka zama ɗan kallo”.
Sosai daddy yaji nutsuwa da kwanciyar hankali. Yanata jerama ɗan ƙanin nasa addu’a da fatan gamawa lafiya kafin su ɗan ƙara tattaunawa yay masa sallama ya tafi. Uncle Yousuf ɗin ne dai yay masa rakkiya kusan har gida. Dan sai da ya ga shigarsa sannan ya juya ya koma yanata sakin murmushinsa da shi jaɗai ya san dalilin kayansa sai kuma UBANGIJI da ke kallon dukkanin motsin zuciyarsa. Koda ya koma gidan maimakon kwanciya sai yay alwala ya nutsu wajen miƙa kukansa da buƙatar neman zaɓin alkairi ga abinda yake ƙudirtawar duk da ba yau ne dama ya fara irin wannan addu’a ɗin ba……
Tofa Uncle You mi kake ƙullawa haka kaima😂🥱?.
★….★
A washe gari data kasance safiyar alhamis a duka ɓangarorin huɗu kowa ya tashi da shirinsa game da abinda ya kwana da shi a rai. Ɓangaren su Hon. HD. Nakowa sun shirya tsaf da shirin zuwa neman auren Mawaddat a wajen Alhaji Sufi Ado Garko kamar yanda ya basu dama. Haka ma a ɓangaren Alh. Sulaiman da ɗansa sun gama tsara komai a daren jiya domin cikar burinsa da kuma burin ɗansa Tajuddeen da ke ƙaunar Mawaddat har cikin zuciyarsa. Ɓangare na uku shine MM Atik Kumo da shima ya tunkari iyayensa da maganar samo mata da yay, sai dai ya gagara tunkararta yana son iyayen nasa su fara zuwa masa neman izinin nemanta ga nata iyayen. Sosai mahaifinsa da Mom ɗinsa suka shiga matuƙar farin ciki, dan babban burinsu dai a rayuwa shine suga auren ɗan nasu daman. Sun samu wannan damar kam bazasuyi sakaci da itaba, musamman ma da sukaji yarinyar ta fito ne da ga zuri’ar Alhaji Sufi Ado Garko da duk wani ɗan siyasa a jihar Kano ke masa kallon uba. Hakama ƴan kasuwa domin a duk ɓangarorin biyu yana taka rawar gani da tarihi bazai iya mantawa da shi ba ko bayan ransa. Rukuni na gaba sune gidan allurar da kowa ke iyo cikin ƙaton kogin domin nema, wato _Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi_.
Mawaddat da tun a daren jiya ta dawo cikin hayyacinta sam bata san duk wannan babban yaƙin basasa da ake shiri a ɓangarori uku domin ita kaɗai ba. Hasalima ita ta wayi gari ne da babban shiri akan mijin matar nan da yay ma yarinya fyaɗe. Har yanzu yarinyar na asibiti cikin mawuyacin hali. Da farko ta hana ƴan jarida yayata zancen har sai ta kama shegen, sai dai a yau wani tunani datai yasa zata bama ƴan jarida damar fitar da komai, tana ganin hakan zai taimaka musu wajen kamashin. Yau da wuri ta kammala shirinta cikin wandon jeans dark blue da milk color ɗin riga. Rigar nada ɗan tsaho musamman ta baya. Ƙaramin veil ta naɗa a kanta tare da bulbula ƙamshin nan nata. Cikin takunta na yanga da izza ta fito, babu alamar jama’ar gidan wani ya tashi, sai su Iya Tabawa dake ta aikin gyaran gidan. Gaisheta suka shigayi cikin girmamawa. Hannu ta ɗaga musu sau ɗaya tai ficewarta dan bata cikin mood ɗin yin magana yau. Karo suka kusan ci da Uncle Yousuf da ke ƙoƙarin shigowa a main falour. Tai saurin komawa baya da faɗin “Sorry Papa ban san ka taho ba”.
“Ina zaki haka?”.
Ya faɗa a dake maimakon amsa maganarta ta farko. Ɗan kallonsa tai da mamaki, sai dai ganin yanda shima ke kallonta babu alamar wasa a tattare da shi ya sata maida kanta ƙasa cikin tsarguwa, dan dama dauriya take kawai, amma tun a daren jiya take ƙullawa da kwancewar ta yanda zata iya haɗa ido da shi, da kuma yanda zata shukama drivern ta rashin mutunci a wannan karon tunda har ya sake bari Uncle Yousuf ɗin ya ganta a cikin wannan yanayin…..
“Baki ji bane? Ina zaki je?”.
Ya sake faɗa cikin katse mata tunani. Firgigit ta dawo hankalinta. Cikin in ina ta ce, “Uncle You office, amma zan fara zuwa nai magana da ƴan jarida akan case ɗin yarinyar nan shiyyasa zan fita da wuri”.
“Shi kuma naki case ɗin kiyi yaya da shi?”.
Da sauri ta ɗago ta dubesa. “Uncle case ɗina kuma? Ni ai babu abinda ya faru da ni”.
“Zai farun ne ai. Biyoni”.
Kamar wadda aka bugama guduma a kai haka Lulu ta tsinta kanta a wannan lokacin. Sai dai bata da zaɓin da ya wuce bin bayan nasa kamar yanda ya bata umarni. Duk abinda ke faruwa Daddy na kallonsu da jinsu. Ya haɗiye hawayen da ke neman zubo masa. A daren jiya ko sau ɗaya baiyi barci ba, sosai jininsa ya hau har bugun zuciyarsa ya fara canjawa. Sai da Mommy ta bashi shawarar yin karatun Alkur’ani sannan ya samu ƴar nutsuwar ganin wayewar gari lafiya. Mommy dai bata san ainahin mike faruwa ba. Amma zuciyarta na bata akan Mawaddat ne, dan a yanzu babu wata damuwa da ke neman kai mijin nata ƙasa sama da al’amarin yarinyar, bayan kuma tun farko shine yay shukar datai tsirran da ya samar da ita a haka.
A falon baƙi da ke a garden kam babu abinda zuciyar Lulu keyi sai bugawa da sauri-sauri. Ga Uncle Yousuf yay matuƙar ɗaure fuska ta yanda bata taɓa gani da ga garesa ba. Zama tai jiki babu ƙari da faɗin, “Uncle gani”.
“Na ganki ai”.
Ya bata amsa shima kai tsaye yana gyara zama. Tambayar da tai matuƙar girgiza mata zuciya ya jefa mata. Babu shiri ta ɗago a firgice ta dubesa. Sake maimaitawa yay babu alamar wasa a tare da shi. “Nace wanene Hon. Haruna Dauda Nakowa a gareki? Miye alaƙarku?”.
“B…b…bamu da wata alaƙa wlhy Uncle”. Ta faɗa cikin in ina da firgici.
“Amma yaje neman aurenki ga Baba a daren jiya”.
“What!! Uncle You aure fa? Ni kuma Mawaddat?!”.
Cikin sigar harara Uncle Yousuf ya bata amsa da “K ɗin fa, bayan shi kuma Tajuddeen ma ya dawo. Dan a jiya mahaifinsa a gabanmu ya sake gabatar da zancen ku ga Baba. Nasan kuma baki manta da alwashi Baba ba na cewar duk wanda yazo neman aurenki ko da amincewarki ko babu ko da tamu ko babu zai aura masa ke. Kinga hakan na nufin a cikin biyun nan dole ne ki zaɓi ɗaya”.
“Wlhy Uncle You bana son kowa a cikinsu. Kuma shi tsinanne Haruna ɗin nan ni ban taɓa magana da shi ba ma balle maganar aure na rantse maka Uncle”.
“Ni wannan ba matsalata bace Mawaddat. Dan a yanzu haka ma Baba nacan na zaman jiranmu ni da ke da Yaya akan wannan maganar dan haka ma na dakatar da ke daga fita. Idan kuma kina da wanda kike so sai ki faɗa mana yanzu mu nemosa aje da shi gaban Baba ki kuɓutar da kanki, dan hakanne kawai zai hana Baba bama ɗaya da ga cikin waɗan can ɗin aurenki kamar yanda kika san shi baya magana biyu”………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣6️⃣
……..“Na shiga uku Uncle, ni ban shirya yin aure ba wlhy. Dan ALLAH ka faɗa mini ya zanyi?”.
“To ni Mawaddat taya zan san ya zakiyi. Yanzun ma na faɗa miki ne dan bana son a miki abinda nasan baki so. Dan Baba bazai taɓa canja ra’ayinsa ba a wannan karon kin sani na sani. Ga kuma Yaya wajen ƙoƙarin ganin ya kare ki sai ya sake wata ɓaranɓaramar wai kina da wanda kike so”.
Fuska ta kuma kwaɓewa idanunta na cika da ƙwalla. “Uncle You wlhy guduwa zanyi”.
“Guduwa kuma? A ganinki itace mafita Mawaddat?. To ai ina ganin dan kin gudu kinyi a banza, dan in dai Baba ne zai aurar da ke ɗin babu fashi ya kuma saka mijin taddaki har inda kika je ɗin ko shi yaje da kansa ya dawo da ke ya danƙama mijin. Kinga anyi ba’aiba kenan ko. Ni dai ina ganin kawai mu ɗauki kariyar da Yaya ya baki muyi amfani da ita dan ki kuɓuta gaba ɗaya”.
“Uncle wacce kenan?”.
“Samo wani matsayin wanda kike so kuma zaki aura. Sai dai ni da ke ne kawai muka san ba haka bane, bayan ƙura ta lafa shike nan sai ki cigaba da sabgarki, idan Baba yayi magana muce iyayen yaron muke jira dan sunce a ɗan jinkirta musu zai ƙarasa gininsa ko dai mu samo wani abu da zai ɗauke hankalin Baba da ga kanki gaba ɗaya”
“Hakan yayi, to amma Uncle kasan fa baba da shegen bin ƙwaƙwƙwafin abu idan kuma ya gano fa?. Sannan ma wa zamu iya samu ya mana wannan aikin batare da an samu wata matsala ba?”.
“Eh kuma fa kema kinzo da maganar dubawa gaskiya. Dan Baba kam zai ma iya sawa ai masa bincike. To amma ina ganin mizai hana shi wanda zamu samar ɗin kawai ki yarda kuyi auren contract da shi, komai mune zamu tsara masa ayi auren amma bayan wata ɗaya ya rabu da ke, sai dai da sharaɗin kada kowa ma yasan ya sake ki har sai bayan wasu shekaru.”
Shiru Lulu tai tana auna zancen Uncle ɗin nata. Sai dai da ace tana da ilimin addini da ya kamata tai hasashen yin hakan fa zai iya zama kamar ta zurma kanta ne. Amma a maimakon hakan ita wani tunani take da ban, dan tana ƙiyasta faruwar al’amarin ne cikin sauƙi kasancewar a inda ta girma cikin turawa wannan ba komai bane yin auren yarjejeniya.. ganin yanda tai nisa Uncle Yousuf ya katseta da faɗin, “Mawaddat bamu da wani isashen lokacin dogon tunani a yanzun fa”. Firgigit ta dawo hankalinta, sai kuma ta langaɓe kai cikin shagwaɓa. “Uncle You ni gaba ɗaya ma kaina ya kulle ne, dan ban san inda zan samo wanda zamuyi hakan ba”.
“To mizai hana ki yarda da batun Tajuddeen kawai, yaron nan yanada hankali da nutsuwa ga ilimi. Yana aikinsa sannan yana matuƙar sonki”.
“Uncle wlhy ni bana son sa, na tabbatar kuma bazan taɓa son shi ba. ALLAH idan aka matsamin kan na auresa zan iya halakash….”
“No! no! Kar na sake jin haka. Tunda har baki sonshi shike nan kawai abar maganarsa. Mu koma kan maganar mu kawai ta nemo wanda zai zame mana makamin kuɓuta da ga Baba.”
“Uncle bazan ɓoye maka ba wlhy na tsani duk wani abinda zai haɗa mu’mulata da wani namiji bayan ku, balle ma ace mu kasance wai ma’aurata. Impossible hakan ya kasance dan bazan taɓa aure ba.”
Har cikin rai kalmar (Bazan taɓa aure ba) ta daki Uncle Yousuf, dan a karo na farko zuciyarsa ta fara hasaso masa wani al’amari mai girma dangane da Mawaddat ɗin. Dolene akwai abinda ya kamata su sani da ke ɓoye a ƙasan zuciyarta, sanin kuma na nufin haƙurin bin matakan daya dace. Wannan tunanin ya sashi cigaba da faɗin, “Mizai hana muyi amfani da Aliyu, dan yaron nada nutsuwar da bazai taɓa iya bamu ciwon kai ba koda anan gaba”.
“Aliyu kuma? Waye shi?”.
*_“DRIVERN KI”_*
Fitar kalmar da ga bakinsa da zaburowar zuciyarta tamkar ragabzane a tsakanin jirgi da jirgi a sararin samaniya. Badan Uncle You bane, da bayan zaburar da tai abinda zai biyo baya shine lailayo masa zagi mai kawuna bakwai ta dire masa shi a tsaye sannan ta tisa da wanke fuskarsa da marin da sai ya hango yanda yaƙin duniya na uku zai kasance tun kafin lokacin faruwarsa. Sai dai kash furucin ya fito da ga bakin da ko harara bazata iya binsa da ita ba balle ɗaukar mataki. Uncle Yousuf da ya zuba mata idanu, sai dai a ƙasan ransa dariya ce ke cinsa yana dannewa da ƙyar yay mata nuni da kujera, tare da faɗin, “Sit mana kika wani zabura kamar wadda na faɗama mummunar magana. Nifa ba nace dole bane, shawarace kawai dan neman mafita. Amma idan batai miki ba muje kawai dan lokaci ma ya cika gashi ana jirana a office. Kije ki zama cikin shiri da yin sabon tunani akan wani tunda naga baki aminta da zancen shi Aliyu ba”.
Bakin data tura gaba ta buɗe zatai magana sallamar Daddy ta dakatar da ita. Alamar zip Uncle Yousuf yay mata wai kar Daddy yaji. Daddy da gaba ɗaya ya gama jin tattaunawar tasu dan tun ɗazun a laɓe yake dama sai ya sake fuskewa cikin pretending ya ce, “Wai mi ake tattaunawa ne kuka shige haka shiru?”.
Cikin ɗan ɗage kafaɗa Uncle Yousuf ya bashi amsa da “Sirri ne tsakanin baba da ƴarsa yaya”.
Dariya Daddy yayi, sai kuma ya juya hanyar fita yana faɗin, “Oh to bari nayi nan tunda ba’a buƙatar naji”.
A karan farko Lulu tai dariya tana mai kamo hannun Daddyn nata cike da shagwaɓa. A haka suka fito suna ƴar dariya…..
Fitowarsu tayi dai-dai da shigowarsa gidan. Kamar ko yaushe sanye yake cikin ƙananun kaya da sukai matuƙar amsar jikinsa. Ƴar ramar da yay ta ciwo ta sashi zama wani fayau da shi a idon mai kallo. Cikin girmama juna ya gaisa da su baba maigadi sannan ya ƙaraso inda suke tsaye. Anan ɗin ma da girmamawa ya gaisa da Daddy da Uncle Yousuf. Lulu da ke gefensu tana danna waya tai jiran jin ya gaisheta amma sai taji shiru. Karo na farko ta ɗago idanunta ta kallesa tana mai sake tsuke fuska. Ƙoƙarin barin ma wajen yake alamar ita bazai gaisheta ba kenan. Wani irin tuƙuƙin baƙin ciki ne da takaici ya shaƙure mata wuya har taji tama kasa yin magana, sai dai yanda take binsa da wani mugun kallo ya sa Daddy farga da ita. Ya kuma fahimci miya fusatata ɗin.
“Aliyu!”.
Yay kiran sunan Smart da ke ƙoƙarin komawa inda su baba maigadi suke. Cikin girmamawa ya amsa yana mai juyowa garesu. Uncle Yousuf da ya sha jinjin jikinsa da tunanin ɓaranɓaramar da Yayan nasa ke shirin yine yay saurin faɗin “Am yaya inaga muje na ajiyekan tunda malam Zaidun bai dawo ba, in yaso daga can sai ya sameka Office ɗin. Aliyu zuwa 1:30 ku samemu a Nasarawa G.R.A please karku makara”.
“In sha ALLAH Alhaji”.
Smart ya faɗa cikin gyaɗa kai abubuwa da yawa na masa kai kawo a rai musamman da Uncle Yousuf ɗin ya ambaci Nasarawa G.R.A. Huci ya ɗan furzar kaɗan, a yanzun ma dai bai kalla inda taken ba ya nufi motar da mai wanki keta faman gogewa alamar ita zasu shiga. Baya ya buɗe mata, batare da ya jira tazo ta shiga ba ya koma mazaunin driver ya shiga yana karanto addu’ar shiga abin hawa. Harta ƙudiri aniyar ƙin shiga, sai kuma mita tuna oho mata ta tako cike da yauƙin nan nata da yanga ta shiga. Mai wanki ya maida motar ya rufe yana jera mata addu’ar dawowa lafiya. Motar yaja suka fice, zuciyarsa cike taf da abubuwan da suka faru jiya a waya tsakaninsa da Uncle Yousuf….
A daren jiya bayan ajiye motar Mawaddat da ya kai sakatariyarta Zainab gida shima gida ya koma abinsa. Kai tsaye wajen Abba ya nufa suka gaisa, sun ɗan taɓa hira da Abban sai dai hirar batai masa daɗi ba sosai kasancewar da ga maganar Hawwah ta juye maganar aurensa. Sosai Abba ya dinga zuba masa faɗa akan infa har bai nemo matar aure ba a cikin watannan tofa shi zai nemo masa da kansa duk da ba aƙidarsa bace yima ƴaƴansa auren dole. Haƙuri shi dai yayta bashi da tabbatar masa cewa in sha ALLAHU zai kawo matar auren nan kusa. Kamar Abba ya gamsu da hakan sai kuma shigowar Umma ta sake saka Abban hayewa sama. Dan kamar wadda dama take a laɓe tana saurarensu tana shigowa sai kawai ta shiga assasa wutar kan cewar shi dai baiyi niyyar yin auren bane kawai. Inba haka ba baga yarinyar maƙwaftansu ba nan Nazifa yarinyar na matuƙar sonshi amma yaƙi saurarenta. Kallonta yay da mamaki, dan kowa dai yasan wacece Nazifa a anguwar. Yarinya ce mara jin magana dan tsabar bleaching fuskarta har yellow takeyi. Tabbas Nazifa ta jima tana nuna masa soyayya, sai dai shi bai taɓa nuna yasan mi takeyi ba. Kai shi ko magana tai masa ma da ga gaisuwa bai sake kulata. Wannan halin watsar da ita ɗin da yake yi yasa tun tana juriyar bibiyarsa har tai fushi ta daina kulashi. Amma da har abubuwa take saye ta aikoma Ammah ko ta bama su Asma’u. Nan ɗin ma dai bata samu nasarar ba dan Ammah tace ita babu ruwanta, idan yaga zai aureta bazata hana ba, za kuma ta bisu da addu’a dan koba komai yayi jihadin raba Nazifa da rayuwar banza da kowa ya shaida tanayi. Yanajin Ammah ta bada goyon baya ya samu Nazifa yay mata gargaɗi na ƙarshen ƙarni ya kuma yima Yayanta magana akan ta fita sabgarsa, shi kuma Yayan yaji haushi ya gaggaya masa magana bai kulashi ba shi dai dan ya yanke magana. Da ga ranar bai san miya faru ba bai sake ganin Nazifa ba. Amma shine dan tsabar sharri Umma ke tisa zancen a yanzu bayan shekara kusan uku kenan da ajiyesa gefe. Tuni Abba ya ƙara tujaresa da faɗa amma baice komai ba akan Nazifa, hasalima ya fahimci kamar faɗan nasa na son zama zargi ne ko minene bai dai fahimta ba. Jiki a sanyaye ya baro wajen Abba, ɗakinsa ya nufa dan bai buƙatar zuwama Amma a wannan yanayin. Ya gama cire kayansa kenan zai shiga wanka kira ya shigo masa. Yayi mamakin ganin Uncle Yousuf, sai da ya kalli agogo ƙarfe kusan sha ɗaya da rabi fa. Haka dai ya daure ya ɗaga cikin taraddadi………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣7️⃣
……..“Alhaji badai wata matsala bace ba ko?”. Ya faɗa maimakon sallama da Uncle Yousuf ɗin yay masa. Murmushi da ga can Uncle Yousuf ya saki tare da gyara zamansa a kujerar falon da ya fito. “Babu komai sai alkairi Aliyu. Wata magana ce mai muhimmanci tasa na kiraka. Ina dai fatan baka kwanta ba na tasheka ko?”.
“Ina dai shirin kwanciyar ne Alhaji. Amma dai lafiya?”.
“Eh lafiya kamar yanda na sanar makan”.
“To Alhamdullahi Alhaji, ina saurarenka”.
Ɗan jimmm Uncle Yousuf yay kafin ya furzar da huci kaɗan. “Aliyu shawara nake nema a wajen ka”. Cike da mamaki ya amsa da, “Alhaji shawara? Sannan kuma ma a wajena?”.
“Eh Aliyu. Kuma ina fatan zaka bani wadda zata fiddani da ga ruɗanin da nake ciki” bai jira cewarsaba ba ya cigaba da faɗin. “Kasan na faɗa maka an taɓa sakama Mawaddat rana da Tajuddeen ai. Amma ALLAH baiyi auren nasu ba wasu matsaloli suka gitta, mafi yawansu da ga Mawaddat ne sai dai kuma akwai ɓoyayyen sirrin saɓani a tsakanin Yaya da mahaifin Tajuddeen da shima ya taka rawar gani. So an share maganar aure kowa ya haƙura, sai dai kakanta na ɓangaren mahaifiyarta Alhaji Sufi Ado Garko ya ɗauki alwashin duk randa wani yazo domin neman aurenta koda yardarta ko babu zai amince masa ya aurar da ita. Wauta ya sata amincewa. Bayan nan magana bata ƙara tashi ba sai a yau ɗin nan a gaban Alhaji Sufi ɗin, shi Alhaji Sulaiman ya sake kawo maganar, amma Yaya yayi saurin cewar ai Mawaddat nada wanda take so………” Tsaf ya kwashe komai ya sanar masa har zancen su Hon. HD Nakowa da Daddy ya sanar masa suma sunje bayan barowarsu. Hakan ya matuƙar bashi mamaki dan tuna abinda ya faru a tsakanin Mawaddat ɗin da su Hon. HD Nakowa. Cikin kasa daure abinda ke bakinsa ya ce, “To amma Alhaji naga kamar ita da shi Honorable ɗin sam basa shan inuwa ɗaya. Taya zaije yace yana sonta da aure?”.
“Muma shine abinda ya ɗaure mana kai Aliyu. Shiyyasa muka kasa zaune muka kasa tsaye akan al’amurin, dan Hon. Nakowa nada ƙarfi sosai a wajen Baba, saboda yaronsa ne, hasalima shine ya zame masa kamar wani ƙashin baya a harkar siyasa.”
“To amma Alhaji mizai hana ku sasanta shi Alhaji Babba da mahaifin shi Tajuddeen ku aura musu juna kawai a wuce wajen”.
“Hakan bazai yiwuba Aliyu. Dan ita Mawaddat sam bata son Tajuddeen, ta tabbatar min idan aka aura mata shi komai zai iya faruwa. Sannan abinda ke tsakanin yaya da mahaifin Tajuddeen abune babba bawai yanda kake zaton zai sasantu cikin sauƙi bane. Kaga ko maganin ayi zumunci ya wargatse ai Gara kar a fara ko”.
“Hakane kuma Alhaji”.
“To Miye mafita Aliyu? Dan Baba fa sam baya magana biyu. In har gobe idan ALLAH ya kaimu Mawaddat bataje da wanda take son aura ba babu fashi cikin biyu dole ayi ɗaya. Shiyyasa ma na kiraka domin neman taimako. Ina son idan ban shiga huruminka ba dan ALLAH Mawaddat ta nunaka a matsayin kai ne zaɓinta, da zaran Baba ya yarda a wajen shikenan. Ni kuma zanyi ƙoƙarin ganin ta fidda miji kafin Baba ya sake magana”.
“Ni kuma Alhaji?!!”.
“Eh dan ALLAH Aliyu ka taimakemu. A yanda rayuwar Mawaddat take yanzu muna buƙatar nutsuwa kafin sama mata mijin da zai saita mata rayuwa. Ni kaina bazan so ta auri Tajuddeen ba duk da nasan mutumin kirki ne amma bazai iya control ɗin ta yanda yake so ko ya kamata ba. Sannan Hon. HD Nakowa, kai ne shedar a inda ka gansu tare, maimakon gyaruwar Mawaddat aurenta da shi sai dai ya ƙarasa lalata ta kawai, shi kuma Baba duk bai san waɗan nan halayyar ba. Amma kaga idan muka kuɓutar da ita a wannan gaɓar sannu a hankali sai irin mijin da muke fata ya samu, kai kawai ta nunakan a gobe shine kawai dan Baba ya aminta ya bar waɗan can ɗin. Amma na baka damar kayi tunani, sai dai bamu da isashen lokaci daren yau ne kawai……
“Wai kai malam ba magana nake da kai ba! Tsabar baka san muhimmancin rayuwa ba kana driving kana ma mutane tunaninka na iska!!”.
Firgigit ya dawo hayyacinsa tamkar wanda aka tada a barci. Sam bai san tunanin nasa har yayi zurfi irin haka ba. Gefen titi ya gangara a hankali tare da kai hannunsa saman goshi ya dafe yana mai furzar da iska. Gaba ɗaya ma ba hanyar da ya kamata yabi da su yabi ɗin ba tsabar hankalinsa bama a tuƙin yake ba gaba ɗaya. Karan farko a rayuwarsa da tunda ya fara aiki matsayin driver ɗinta ya furta mata “Am sorry”. Cikin tausasa harshe kuma. Cak numfashin Lulu ya nema tsayawa a ƙirjinta. Haka ma maganar bakinta kasa ƙarasa fita tai tsabar kalmar ban haƙurin tazo mata a matuƙar bazatar da bata taɓa tunanin hakan da ga bakinsa ba kasancewar kallon da take masa mai shegen girman kai. Har ya sake tada motar da juyawa bata iya sake yin ko tari ba kamar wadda aka ɗinke ma lips. A nashi ɓangaren bai kawo komai game da shirun nata ba, a tunaninsa maganar Uncle Yousuf ce ta jiya ke damunta kamar yanda shima da ya kasance ɗan karoro kawai a ciki take neman jefa shi a ɗimuwa. Har suka isa office babu wanda ya sake magana. Kafin kuma ya fita ya buɗe mata har ta buɗe ta fice. Kallo ya ɗan bita da shi, dan duk da yau ma dai irin kayan daya tsani gani a jikin mace tana yawo kan titi ne a jikinta ɗan zoɓawar rigar da ga baya ya taimaka wajen suturta wani ɓangare na jikin nata. Janyewa yay tare da furzar da huci. Dai-dai nan Zainab ta fito ɗaukar mata kaya dan babu abinda ta ɗauka tai shigewarta. Ganinsa ya saka Zainab yin murmushi, ta risina cikin girmamawa ta ce, “Yaya ina kwana”. Kalmar yaya da ta kirashi da shi ce ta sakashi maida mata da murtanin murmushin nata itama. Cike da kulawa ya amsa mata kuma. Handbag ɗin Lulu da laptop da riga ta ɗauka sai wasu tarkacen takardu, shi kuma ya fito a motar tare da kulleta ya nufi security ɗin nan na jiya dan su gaisa…..
Duk yanda Lulu ta so fuskantar aikin gabanta hakan ya gagara. Abubuwa ne da yawa ke cizon zuciyarta musamman shawarar Uncle You da yace ta nuna drivern ta matsayin wanda take so a gaban Grandpa ɗinta. Kai ina a gareta wannan ai ƙasƙanci ne ma, kenan ma ya samu hanyar cigaba da kawo mata raini fiye da wanda yake son gwada mata a yanzu, dan ma dai ita tsayayya ce yana shakkarta. Kai maganar gaskiya shawaran nan na Uncle You baiyi ba sam. To amma a yanda guri ya ƙure ɗin nan idan ba shi ba wa zasu samo yay musu aikin batare da an samu matsala ba?. Wannan tambayar ita ta shiga cizon zuciyarta tama kasa iya aiwatar da komai na gabanta. Tana buƙatar shawara, gashi ƙawarta kuma Nadiya ce kawai da har take iya faɗama damuwarta. Kai ina bazata kira Nadiya ba, dan sai ta koya mata hankali. Kai anya ma bada saninta wannan tsohon kwandon Hon. Nakowa yazo neman aurenta ba? Lallai akwai lauje cikin naɗi, dan zuwa yanzu ta fara shakkar al’amarin Nadiya, ita shiyyasa fa bata ƙawa musamman da ya zam ƙawaye sun taka rawar gani suma wajen bar mata wani tabo a zuciya da har yanzu gyambonsa ke kan yin ruwa da mata ciwo. Kodai Uncle Yousuf zata kira ne tace ta fasa a nema wani? Aminta da wannan shawarar ya sata kiransa.
“Lafiya dai ko Daughter!”.
“Uncle you ba lafiya ba, shawaran nan ne yaƙi zama a zuciyata. Kodai mu nema wani can daban yay mana aikin nan, kasan fa bana son raini”. Murmushi yay da ga can har tana iya jiyo sautinsa. “Mawaddatan’warahma!”. A hankali ta amsa da “Da yes papa”. Dan tana matuƙar son ya kirata hakan.
“Ki kwantar da hankalinki Please, sannan ku tuna bamu da wani isashen lokaci, a yanzu haka fa awowi kaɗanne suka rage mana dan za’ai amfani da ɗan break na lokacin sallah ne wajen zaman meeting ɗin kafin kowa ya koma office. A tunaninki a irin wannan tsukun lokacin wa zamu samu mai amana da hankali kamar Aliyu da zai mana aikin nan batare da wata matsala ba? Ko kina son mu ɗakko wanda zai mana baragada har Baba ya gane ya zartar miki da hukuncin auren ɗaya da ga cikin waɗan da baƙya son?”.
“A’a Uncle You… ALLAH idan yace sai na auri wani a cikinsu zaku iya rasani dan na tsane su”.
“To mafita ɗaya ce ta kufce musu shine bin abinda muka tsara. Shin kin san da yaya ma shi Aliyun ya amince zai mana aikin? Da ƙyar fa na iya shawo kansa wlhy”.
A zuciyarta ta ce (kuji ɗan iya, dama ya samu aka sakashi zai wani kawowa mutane iyayi. Mtsowww banda ma dai wannan Grandpa ɗin da matsalarsa shi ko’a mafarki ya isa ma na kallesa balle wani kalman so can na wofi. Bari ana gama zaman nan korarsa zanyi dan karma ya ɗauka ya samu wata damar kawo min raini…..)
“Hello Mawaddat! Kina jina kuwa?”.
Ajiyar zuciyar dawowar hayyaci ta saki, cikin shagwaɓa ta ce, “Shike nan Uncle sai mun haɗu”.
Dariya yay sosai daga can bayan ya katse kiran. Dan harga ALLAH dariya suke bashi. Dama yanzu ya gama waya da Smart ɗin shima. Haka kawai sun sakashi komawa lauyan dole. Ya tsara wannan ya tsara wannan. ALLAH dai ya bashi nasara burinsa ya cika akan abinda ke ransa game da su su duka biyun……..✍️
🥱Ba abun faɗa.
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣8️⃣
…….Ƙarfe ɗaya da minti biyar ta fito da ga office saboda kiran da Uncle Yousuf yay mata da gargaɗin karfa su makara. Kamar ko yaushe babu kwalliya a fuskar tata, sai dai an toshe idanu da glass. Tabbas glasses na mata matuƙar ƙyau shiyyasa da wahala ka ganta babu shi, gashi bata saka ƙarami sai in zatayi aiki. Duk irin manyan nan ne na manyan mata masu ji da gayu. Shima ɗin dai kiran Uncle Yousuf ɗin ne ya sashi dawowa, dan tun kusan sha biyu ya wuce gida. Yanzu kam ya canja kayansa zuwa shadda ash color da tai masa matuƙar ƙyawun da har ita sai da ta saci kallonsa irin wanda bata taɓa yi ba. Dan tunda ya fara tuƙata bata taɓa ganinsa da manyan kaya ba sai yau har da su hula. Gaba ɗaya sai ya sake mata wani kwarjini da cika waje, dan haka ta sake jan girma tai tamau da fuska tare da ɗauke kai sama kamar bata gansa ba. Ita a dole kar waccan maganar tasa ya kawo mata wargi tunda Uncle Yousuf ya tabbatar mata ya sanar masa. Shima ɗin dai tasa fuskar a ɗauren take, dan baya son ta taresa da wata maganar banza, ta wani ɓangaren kuma ransa ne a ɓace, dan zuwa gidan nan da yay ya samu Umma na tujara harda yima Ammah gori akan ƙaddararsa wai a bincike wannan ƙin auren nasa sai dai idan yana samun abinda auren ne kawai zai iya bashi a bayan fage. Kenan tana nufin shi ɗin mazinaci ne. Bai san miya kawo rikicin ba, bai kuma shiga gidan ba yaji ba’asi tunda muryar Umman kawai yake ji, dama kuma yasan Ammah bazata tanka mata ba. Ganin Lulu ta dogare tana wani huhhura hanci irin na ubangida da yaronsa ne sashi jan ƙaramin tsaki ciki-ciki, batare da yace komai ba ya buɗe mata ƙofar, shiga tai fuska a yamutse, shi dai baibi takanta ba ya maida ya rufe sannan ya koma mazaunin driver.
A hankali yake murza steering Lokaci-lokaci yana ɗan furzar da iskar takaicin kalaman Umma da sukai masa kane-kane a zuciya. Yayi nadamar zuwa gidan nan ma….
Kusan lokaci guda suka iso da su Daddy, dan haka Uncle Yousuf ya dakatar da shi a gate, fita yay a tasu motar yazo inda suke. Lulu da keta ɓata fuskar shagwaɓa ya kalla. “Mawaddat ya haka kuma? Maza koma gaba karma wani ya ganki”. Zatai magana yay mata nunin tai shiru kawai ta koma. Fitowa tai baki a sama ta koma gaban, kusan a tare ƙamshin turaren junansu ya daki hancinansu duk da dama tun ɗazun suke shaƙar. Shi dai baice komai ba, hakama Uncle Yousuf ya koma tasu motar shima, sun samu ƙaton compound ɗin gidan cike da motoci, ya dai samu gefe yay parking. Hango Uncle ɗinta Khamil na Abuja ya sata sakin murmushi, cike da zumuɗi ta buɗe motar ta fita…. Baki ya taɓe tare da ɗauke kansa. Sai ma ya lumshe idanunsa kamar mai shirin barci tare da kwantar da bayansa a jikin kujerar yay luf…
Suna shiga aka fara taron dan kamar sune dama na ƙarshen zuwa. Ana tsaka da tattauna batun Tajuddeen ɗin da Lulu da aka kira amma ta botse musu akan ita fa bata son Tajuddeen, shi ko ya marairaice fuska kamar zai fashe da kuka yanata faman mata alamar roƙo amma tai kamar bata gansa ba. Takaici ya saka Alh. Sulaiman fara zagin Mawaddat ɗin, ana hakan saƙon isowar su Hon. Nakowa ya iso falon. Damar shigowa Baba ya basu. Su ukune kamar dai jiya. Shi mai gayya mai aikin Hon. HD Nakowa da aminansa Hon. Misau da Alh. Baita. Bayan anyi gaisuwar mutunci tsakaninsu da su duk da Alh. Sulaiman yayi mamakin ganinsu a gidan nasu Baba ya gabatar da su da dalilin zuwansu cikin meeting ɗin tare da buƙatarsu. Shiru falon yay kamar waɗanda ruwa ya cinye. Sai Lulu ce ke antayama Hon. Nakowa harara tamkar idanunta zasu zubo ƙasa. Cikin katseta Baba ya kirayi sunanta. Amsawa tai tana ƙoƙarin danne fushinta. Baba da ya gama lura da duk hararar da take antayama Hon. Nakowan ya cigaba da faɗin, “Bayan maganar Tajuddeen ga Hon. Haruna. Nasan shima dai kin sanshi tunda yace kece kika turosa wajenmu kamar yanda Mahaifinki ya tabbatar mana dama akwai wanda kike so”.
Da sauri Lulu ta kalla Hon. Nakowan, cikin fushin da ya fara fallasa kansa a maƙoshinta ta ce, “Baba ni bamma san wannan mutumin ba face a poster. Magana kuma bata taɓa haɗani da shi ba kota gaisuwa balle zancen soyayya. Ni bashi bane wanda nake so kuma shi yana a waje”. Maganar ƙarshen ta fito a bakinta cikin suɓucewar harshe da ita kanta sai da ta gama faɗa ta tsinta kanta cikin matuƙar takaicin kan nata. Dan haka ta wani yatsine fuska, a zuciyarta tana faɗin (ALLAH ya kiyaye naso driver na can dai)…
“Waye shi? Miye sunansa? Ɗan wanene kuma?”.
Jerarrun tambayoyi da ga bakin Alh. Sulaiman cikin makirci da shirin da ya kammala tsarawa tsaf tun a daren jiya, dan ya ɗauki alwashin ƙararma da Daddy man kai tsaf kasancewar yana ji a ransa shirine kawai, dan a bibiyar da yake ma Mawaddat ya tabbatar bata da wani saurayi, duk wanda ma ya raɓeta da batun soyayya yagashi takeyi. Uncle ɗin nata ta kalla a ɗan daburce, sai dai kafin tace wani abu Baba da hankalinsa ba’a kanta yake ba balle ya fahimci halin da take ciki ya furta “Jeki shigo da shi”. Kamar wadda dama take jiran umarnin, zumbur kuwa ta miƙe ta fice. Har yanzu yana kwance a motar, sai dai saɓanin ɗazun yamzu karatun Alkur’ani yake saurare a wayarsa. Darajar waɗan da ke ɗan kai kawo da gudun kar wani ya ganta ya sata masa knocking a hankali. Tun fitowarta ya riga ya ganta, tsaiwarta a wajen da hararar data dallarama motar wadda yasan tasace kuma duk a kan idonsa ne. Amma sai yay buris har sai da ta ƙara na biyu cikin ɗan fara tunzura. Gilashi ya sauke ƙasa a hankali, babu zato idanunsu suka shige cikin na juna. Kusan a tare suka janye da sauri, ita tana jan tsaki da ƙarewa da kwafa.
“Sai ka fito malam. Saura kuma idan ka shiga kaima mutane ƙauyancin da ka saba. ALLAH sai na koya maka hankali”.
(idan baki koyamin ba ni zan koya miki) ya faɗa a zuciya, a zahiri kam kansa ya gyaɗa mata kamar wani salihin gaske (😔🥱) itako sai taji kan nata ya ƙara girma. Matsa masa tai ya fito tana watsa masa hararar ƙasan ido. Shi dariya ma ta bashi, amma sai ya kanne, a ransa kam ya riga ya gama tsara haukan da zai manna mata a ciki, dan ya gama shirya kwance mata zani a kasuwa, ya san dai Uncle Yousuf zaiji ba daɗi, zai bashi haƙuri kawai a wuce wajen dan gaskiya shikam ba za’ai wannan aikin rashin gaskiyar da shi ba. Dan garama ya zame kan nasa kakan nata yay mata auren dolen da shi yafi dacewa da ita ma kodan tarbiyyarta da ke ƙara neman taɓarɓarewa. A jere suka tafi tana wani ɗan murmushin da iyakarsa lips. Shima kuma yana murmushin muguntar da ya gama shirya mata. A nutsensa yay sallama. Duk da yawan mutanen da ke a farlon baiji ko ɗar ba a ransa, sai ma gaishesu da yay a jimlace cikin cikar kamala. Da yawa ya burgesu, sun kumaji a aransu lallai Mawaddat ta iya zaɓe, ashe girman kan nata da izza bazai ƙare a banza ba irin wannan hot guy haka. Tajuddeen kam sumar zaune yay kansa a juye, haka suma su Hon. Nakowa idanu kawai suka zuba masa cike da ɗimuwar rashin makamar yin tunani. Baba ne yay murmushi bayan ya gama ƙarema masa kallo da ga sama har ƙasa cikin ƴan sakkani. Cike da dattakonsa ya nunama Smart gefensa da faɗin, “Ƙaraso nan ka zauna kaji my Grandson”.
Baiyi musu ba ya ƙarasa garesa, sai dai maimakon inda ya nuna masa sai ya zauna a ƙasa gaf da ƙafafunsa dan haka kawai tsohon yay masa wani irin masifaffen kwarjini. Murmushi mai ma’anoni da dama Baba ya sake saki, haka ma Uncle Yousuf. Cikin tsantseni da noƙewa ya sake gaishe da Baba da ya miƙo masa hannu alamar su sake gaisawa. Nan ma murmushin Baba ya sake yi da faɗin, “Shike nan tunda baka so mu samu ladan juna. Minene sunanka yaro na?”.
“Aliyu Hydar M. Idris Mawashi”.
Ya bama Baba amsa cikin girmamawa. Kai baba ya jinjina da faɗin, “Masha ALLAH suna mai daraja. ALLAH yasa kayi koyin ainahin mai sunan. Ali mazan fama, Ali gadanga ƙusar yaƙi. Ali zaki, Ali sadauki.”
Kirarin da Baban yay masa ya saka wasu da yawa sakin murmushi a afalon ciki harda shi kansa Smart ɗin. Baba ya cigaba da maganarsa kai tsaye. “Sadauki minene alaƙarka da jikata Mawaddat?!”.
Wani irin bugun ƙirjinsa tambayar tayi har acan ƙasan rai, amma sai ya dake cike da bama kai ƙwarin gwiwa ya ɗago kaɗan da nufin kallon Lulu cikin ido ya bama Baba amsa da (babu komai) amma aka samu akasi a bazata idanunsa suka sauka akan mutumin daya saka aka satoshi, ya kuma damƙa masa aiki akan Jiƙamshi family. Cikin ido suka kalla juna shi da Alhaji Sulaiman Sufi Ado Garko da shima ya kafeshi da idanu cikin wani irin yanayi mai wahalar fassara. Matuƙar girgiza Smart ya shiga, sannan mamaki ya nema halaka shi, (wanene shi anan ɗin?) Zuciyarsa ta ayyana masa bayan ya janye idanunsa. Bashi da mai bashi amsa, sai dai yana da damar neman amsar ta dalilin amsar da zai bama Baba a yanzu. Dan haka kai tsaye ya furta, “Ranka ya daɗe alaƙar soyayya da muke fatan ta kaimu ga aure. Kuma harta yarjemin turo magabatana duk da kasancewar baka nan ya kawo tsaikon hakan”..
“Masha ALLAH Alhamdullah, ai yanzu gani na dawo. Mawaddat! Ga Tajuddeen, ga Haruna, ga kuma Aliyu Hydar, wanene zaɓinki? Ina son ki faɗa ko nace ki sake faɗa a gaban kowa domin samun daidaito da rufe wannan babin mu fuskanci na gaba”.
Da ƙyar Lulu ta haɗiye yawun takaicin Smart da ya maƙure mata maƙoshi da cimata zuciya. Ta ɗan dubi inda Uncle Yousuf yake, cikin sa’a ta samu ita yake kallo sai ya gyaɗa mata kai a yanayin bata ƙwarin gwiwa. Ajiyar zuciya ta sauke a ɓoye, tare da danne zafin da takeji da ƙyar ta gyaɗa kanta da faɗin, “Grandpa ni shi nake so”.
“Wa ɗin?”
Sai da ta rumtse idanunta sannan ta furta “Hydar” a hankali kamar mai raɗa………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣9️⃣
……..“Ƙarya kike yi munafukan yarinya”. Alh. Sulaiman ya faɗa cikin suɓucewar baki. Yayinda Daddy da Uncle Yousuf suka saki wata irin ajiyar zuciya a ɓoye. Shiko Smart ƙirjinsa ne yay wata irin yankawa har sai da ya lumshe idanunsa yana mai ambaton sunan ALLAH. Furucin Alh. Sulaiman dana Tajuddeen da shima a zabure ya furta, “What! Drivern naki? Kai ina wlhy ƙarya kike Mawaddat akwai wani shiri a wannan zancen naki”.
Falon ne ya nema ruɗewa kowa na ƙoƙarin faɗin albarkacin bakinsa. Yayinda Smart ya dilmiya cikin kogin ninƙayar nazari. Dan abinda Alh. Sulaiman ɗin yayi ya sake zaburar da shi ne har wasu abubuwa masu girma da ya gama tsara gujemawa suka fara bijiro masa. Tsawatarwar Baba ta saka falon yin shiru. Hakan ya sake bama Smart da Alh. Sulaiman damar yin kallon kallo, kai tsaye Smart yake nazartar gargaɗi mai firgitarwa da ga idanunsa, dan haka ya sakar masa wani shegen murmushi da masa alamar 1-0 ya kashe ido ɗaya. Rawa jikin Alh. Sulaiman ya fara, sai dai ƙoƙarin ganin ya nutsar da kansa yake. Ganin fa hakan bazai faruba ya sashi miƙewa a zabure ya kama hannun Tajuddeen suka fice. Babu wanda ya hanasu. Ganin haka ma sai suma su Hon. Baita suka ce zasu wuce. Godiya Baba yay musu da basu haƙuri yana mai sake tabbatar musu bazai ma Mawaddat auren dole ba. Amma yana mai basu haƙuri tare da dama idan har akwai wata da Hon. Nakowa zai iya so a cikin zuri’arsa bayan Mawaddat ya bashi dama yazo ya sake gwada sa’arsa su dai-daita”.
Godiya sukai masa da tabbatar masa yin nazari akan maganar tasa, suka kuma yi fatan alkairi ga Mawaddat ɗin duk da dai ta ciki fa na ciki. Bayan wucewarsu Baba ma addu’a ya saka ayi ya sallami kowa, sai dai banda Daddy da Uncle Yousuf da Smart. Amma har Lulu yace taje. Koma ba’ace taje ɗin ba batai niyyar zama ba, dan in har ta cigaba da zama a falon zata iya aikata ɓaranɓaramar da komai zai tashi a wajen….
Tambayoyi na mutuntawa Alhaji Sufi Ado Garko ya sake yina Smart, shiko ya amsa masa cikin nutsuwa kuma kansa tsaye. Hakan ya saka Uncle Yousuf jin farin ciki, sai dai umarnin Baba na ƙarshe akan Smart na cewar ya je ya sanar ma iyayensa suzo a cikin satin nan ya girgiza Daddy matuƙa har ya ɗan waro ido sai da Uncle Yousuf ya zunguresa. Shi kansa Smart maganar ta girgiza shi, dan da ƙyar ya iya haɗiye yawu ya gyaɗa masa kai…..
🤣Wayaga cakwakiya mai taurari. Kai Smart ka ɗauka abin wasa ne kenan, ai gashi nan Baba yay maka ɗaurin huhun goro 🤪🚴.
★★★…..
“Kai Yousuf bazai yiwu ba. Ina bazan taɓa yarda Mawaddat ta auri yaron nan ba gaskiya. Da ace nasan wannan shawarar ka yanke dana kwaɓeka tun farko. To gashi nan DAGA WASA KARAMAR MAGANA NA NEMAN ZAMA BABBA. Dama kai kana tunanin yin wasa da hankalin Baba ne?”.
Daddy ne mai wannan magana cikin tashin hankali da damuwa wa Uncle Yousuf da ke driving. Cikin dakewa da nuna alhini kamar gaske shima Uncle Yousuf ɗin ya ce, “Yaya sam ba haka nai tunanin kasancewar al’amarin ba fa. Banyi zaton zaice Aliyu ya turo magabanasa da wuri kamar haka ba. Shima fa yaron da ƙyar na shawo kansa ya yarda zai mana aikin. Ni yanzu ma gaba ɗaya kaina ya kulle na rasa mima ya kamata nayi”.
“Faɗama Baba gaskiya mana. Dan nasan Mawaddat bazata taɓa yarda ta auri drivern ta ba. Kai koni ma hakan bai min ba Yousuf. Ina impossible kamar yarinyata mai daraja irin Mawaddat ta ƙare da auren drivern ta, sai kace wani almara ma”.
Ɓacin raine sosai ya dunƙule zuciyar Uncle Yousuf, cikin matsanancin takaici yake duban Yayan nasa, sai dai baiyi magana ba ya sake maida kansa ga titi har suka isa gida. Shima Daddyn ya fahimci ran ƙanin nasa ne ya ɓaci, amma bai fahimci ainahin miya ɓata masa ran ba. Suna isa gida Uncle Yousuf baiko fita a motar ba yay shirin juyawa. Da mamaki Daddy da ke kallonsa ya furta, “Ya zaka koma kuma bamu gama magana ba Yousuf”.
Idanu Uncle Yousuf ɗin ya rumtse sai kuma ya buɗesu akan Daddy. “Yaya to wace magana kuma ta rage? Kace bazata auri driver ba, shike nan magana ta ƙare ai, dan ni kam iya abinda zanyi nayi k….”
“Kaga sakko muje ciki wannan ba maganar mota bace.” kamar zai ce a’a sai kuma dai yabi umarninsa ya fito. Falon baƙi suka nufa, dan in har zasu maganarsu ta sirri sunfi buƙatar zuwa can kasancewar babu wanda zai iya jinsu. Suna shiga Daddy ya ce, “Yousuf ka fahimceni mana. Ni fa ba ina nufin bakai ƙoƙarinka bane ba. Amma Please ka duba mana. Yaron nan fa driver ɗinta ne….”
“Shi driver ba mutum bane? Ko kuwa shi dama mai arziƙi ALLAH ya tabbatar masa shine mafifici ga kowa a duniya da da lahira?. Gaskiya yaya ka fara bani tsoro, matuƙar tsoro ma kuwa. Wai kai kuwa wani irin so mara fasali kake ma Mawaddat? Ko kai ne zaka aure ta….”
“You’r vary stupid Yousuf! Wane irin banzan magana ne wannan?”.
“Dolene na faɗi hakan ai Yaya. Dan al’amarin naka ya fara wuce makaɗi da rawa kuma. Idan ka manta shekarun Mawaddat ashirin da huɗu har da watanni balle kace bata isa aure ba. Tun tana shekara ashirin aka saka mata ranar aure ka goya da bayanta al’amarin ya wargatse. Idan kace wancan yana da wani aibu shi wannan minene aibunsa? Dan kawai ya kasance driver mai neman halaliyarsa? To wlhy bakai ya kamata kace Mawaddat tafi ƙarfin Aliyu ba. Aliyu ne ya kamata yace yafi ƙarfin Mawaddat kodan halin da take a ciki wanda kai ne gaba-gaba wajen zama silarsa. Kai ne ya cancanta kai ƙoƙarin ganin ka gyara ko neman hanyar da zata gyaru ta zama cikakkiyar mutum kafin kowa amma baka ƙoƙarin yin hakan sai sake bata damar ma da zatafi yanzu lalacewa kake yi. Ina ji maka tsoron ranar da Baba zai fahimci halin da Mawaddat take a ciki, in dai maganar Aliyu ce kuma na bari…..”
Da sauri Daddy da jikinsa yay sanyi ya riƙoshi. “Kaga kayi haƙuri auta.”
Batare da Uncle Yousuf ya yarda ya juyo ba ya ce, “Kai zan bama haƙuri ai Yaya. Dan na shiga hurumin daba nawa ba. Na manta Mawaddat ƴarka ce kai ɗay….”
“Shiiii! Ni ba haka nake nufi ba auta. Amma tunda zuciyarka ta kaika ga hakan amin afuwa. Ni kaina wani lokacin yanda nake ɗaukar al’amarin Mawaddat na bani tsoro. Amma dan ALLAH ka tayani da addu’a. Sannan kayi haƙuri ka cigaba da duk yanda kake ganin shine dai-dai. Ba Mawaddat ba ko ni ka isa dani ai ko. Wlhy a duk sanda kake faɗamin gaskiya akan lamarin Mawaddat fuskar Mahaifinmu nake gani akan fuskarka, yayinda muryarka kan juye min tamkar ta mahaifiyarmu. ALLAH yay maka albarka auta. Ina alfahari da kai a matsayin ɗan uwana da ga kai har Kareema. Wlhy itama fahimtata ne kawai batayi tun farko, amma tana da wata daraja da kima mai girma a gareni”.
Tsira masa idanu kawai Uncle Yousuf yay kalaman nasa na bashi mamaki da al’ajabi. Anya kuwa Yayan nasa bashi da Alhaju? Dole ne yace haka, dan yau wai bakin Yayansa ne ke yabon Aunty Kareema. Kai anya kuwa dai…..
Kamar Daddy ya fahimci abinda ke a ran ɗan uwan nasa ya saki murmushi mai ciwo. “Mamaki kake ko auta? Kana mamakin yabon Kareema a baki na. Humm bazaku gane bane, dan tun farko bakubi hanyar da zaku gane ɗin bane shiyyasa kuke min kallo irin wanda bashi ya kamata kumin ba. Kaje kawai abinka. Na kuma maka alƙawarin bazan sake saka baki ba akan al’amurin auren Mawaddat dan kai ne ubansu dama ni ɗan kallo ne. Sai dai a wannan gaɓar ina tunatar da kai suma su ƴan biyu ya kamata ka sakasu suyi aure fa. Kaje ALLAH ya huta gajiya”. Da ga haka Daddyn ya fice idanunsa taf da ƙwalla. Da kallo kawai Uncle Yousuf ya bisa zuciyarsa na kaikawo a ƙirji. Dan ba ƙaramin ratsa masa zuciya kalaman ɗan uwan nasa sukai ba yau……
★★….
A ɓangaren Lulu da bata san hukuncin da Baba ya yanke ba suna fitowa a street ɗin gidan Baba a gadarance ta cema Smart “Malam tsaya da motar nan”. Kamar zai shareta sai kuma ya gangara dan yanzu ba shirmenta bane a gabansa. Abubuwa ne masu yawa ke masa kaikawo a zuciya. Fita tai ta koma baya, bai ce komai ba ya sake tada motar suka cigaba da tafiya. Sun ɗan ƙara nisa motar shiru babu mai magana, shi hankalinsa ya rabu biyu, wani a tuƙi wani a tunanin al’amarin da ya faru yanzun nan. Ita kuma hankalinta nakan tab… Ɗinta ne tana aiki har suka iso. Ita ta buɗe da kanta dan hankalinta nakan abinda takeyi, sai da ta zura ƙafarta ɗaya waje zata fita sannan tai magana batare data kallesa ba. “Malam ina fatan baka ɗauki abinda ya faru a gidan Grandpa wani abu ba. Idan kuma ma ka ɗauka ɗin to ka ajiyeshi a motar nan karma ka koma gidanku da shi dan zai zame maka dakon wahala ne, dan ba Mawaddat ba ko mai aikin gidanmu tafi ƙarfin nunaka matsayin abin sonta balle ni, ka cigaba da zama matayinka na yarona kana amsar albashinka hankali kwance a samu na koko da ƙosai”. Ta ƙare maganar da balla masa uwar harara da jan tsakin tabbatar da gargaɗinta ganin yanda ya wani tsareta da idanu ta cikin mirror. Kansa ya ɗan girgiza bayan ficewar tata, sai kuma ya saki wani shegen murmushi da cije lips ɗinsa yana mai kai hannu ya shafa tattausar sumar ƙasumbarsa. A hankali ya furta, “Kema lokaci yayi da zaki fara cin koko da ƙosan ai ƴar gidan madara”. Ya ƙara cije lips ɗinsa da kashe ido ɗaya….
(Makiri Smart. Mi kake shirya mana ne🥱😨).
______________________
“Dad! Wlhy wannan abun ƙarya ne shiri ne kawai. Amma babu wata soyayya a tsakanin Mawaddat da shi. Drivern ta ne fa, hasalima Alhaji Yousuf dani muka zauna muka roƙesa akan ya tuƙata saboda muna son ya bibiyar mana al’amarinta akan s…..”
Sai kuma yay shiru tuna ɓaranɓaramar da yake neman yi ga kallon da mahaifin nasa ya kafesa da shi. “Ya ka dakata? Ƙarasa mana akan mi?”.
“No Dad share. Wannan bashi bane mai muhimmanci, musan gaskiyar zancen da tabbatar ma Grandpa shine nafi buƙata a yanzu. Idan ba hakaba wlhy sai na tada hankalin kowa a family ɗin nan dan Mawaddat kaɗai nake so, da ita kawai nake buƙatar zaman aure”.
“Tajudden ka kwantar da hankalinka, in dai Mawaddat ce babu fashi kai ne mijinta. Yaron nan kuma nima na tabbatar sakashi akai ko kuma shine ya sa kansa. Amma barni da shi, zan tabbatar masa wanene ni dan naga yana son yin wasa da wuta ne a tafin hannunsa batare da ya sani ba. Kaje ka cigaba da shirye-shiryen aurenka nan da kwanaki takwas”.
“Amma miyasa ba gobe ba Dad? Ni gobe nake so Friday a ɗaura. Next Friday ai shagalin biki na nunawa Sa’a ta tare a gidana.”
“Ka ɗauka yanda ka tsara labarin, haka za’a bugashi a jaridu da mujallu a yammacin gobe cewa Tajuddeen Sulaiman Sufi Garko ya zama angon Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi”.
“Thanks You Dad”.
Tajuddeen ya faɗa cike da zumuɗi yana mai rungume mahaifin nasa, dan yasan baya magana bai tabbatar da ita ba……
Gaba ɗaya tattaunawar ɗa da mahaifin acikin kunnenta ne, dan tun farawarsu ta iso ƙofar falon bisa umarnin auntynta da ta aikota. Da sauri ta tallafe tray ɗin dake hanunta mai ɗauke da kayan motsa baki jin zai suɓuce mata. Juyawa tai da sauri zuwa apartment ɗin yayarta cikin sassarfa kamar zata faɗi ga idanunta na kwarar da hawaye masu zafin gaske……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣0️⃣
…….“K! K! Lafiya kuwa naga kin dawo min da shi haka kamar ma wadda take a firgice?”.
Ƙasa ta dangwarar da tray ɗin tare da faɗawa jikinta ta sake fashewa da kuka. “Aunty Abasiyya wannan karon ma zan rasashi. Dama ashe abinda ake ƙullawa a gidan nan kenan amma baki faɗamin ba kika barni inata shirme na?” ta ƙara fashewa da kuka. “Mtsoww! Wai nikam Ramlah yaushe ne zaki hankali? Kimin bayani danni ba fahimtarki nake ba. Kinga tashi zaune”. Babu musu Ramlah ta tashi, ƙyaƙyƙyawar yarinya kuma ƴar gaye. Bata damu da share hawayen da suka gagara tsaya mata ba, ta ce, “Aunty Abasiyya zaki cemin baki san shirye-shiryen auren Tajuddeen ake ba a gidan nan kuma da mayyar yarinyar can dai”.
“What! Auren Tajuddeen fa? A gidan nan kuma ban sani ba? Lallai Alhaji ya sake zama abinda ya zama. Wlhy Ramlah sam ban san da zancen ba, sai dai tabbas naga anata wani ƙus-ƙus tsakaninsa da matarsa na munafunci tun jiya, yau kuma ya ɗauketa suka fita sai dai ban san ina sukaje ba”.
“To Aunty babban gida sukaje, dan inaga Baba ya dawo…..”
Ta kwashe kaf abinda taji Tajuddeen da babansa na tattaunawa ta sanar mata. Tare da faɗin, “Aunty dan ALLAH ki taimake ni, wlhy idan na ƙara rasa Tajuddeen a wannan karon zan iya rasa rayuwataa gaba ɗaya ina sonsa matuƙa fiye da yanda nake son kaina”.
“Hummm Ramlah kenan, badan nasan minene zafin soyayya ba da nace baƙya kishina. Ina matsayin yayarki uwa ɗaya uba ɗaya amma kina son ɗan kishiyata da bata taɓa ƙaunata ba a gidan nan, da ace ma tanada dama da tuni ta kawar dani a duniya. Gaskiya wannan soyayyar taki bataimin adalci ba. Sai dai bazanƙi taimakonki ba, dan nima hakan zai taimakeni wajen ƙuntata rayuwar Hajiya Turai. Dan haka ki kwantar da hankalinki, yanzun nan zan warware musu ƙullin nasu ta inda basu taɓa zato ko tsammani ba.”
Cike da ɗoki Ramlah ta ce, “Aunty mi zakiyi?”.
“Jira ki gani”.
Ta faɗa tana janyo wayarta. Daddanawa tai takai kunne tare da miƙewa ta shige ciki tana faɗin, “Baba barka da rana…….” iya abinda Ramlah taji kenan…..
★ Alhaji Sulaiman kam da basu san Ramlah ƙanwar amaryarsa da take riƙo taji tattaunawar tasu ba tuni Tajuddeen ya fice da waya a kunne yana waya da telansa kan ya jirashi a shago yanzu zai zo da ɗinkin ujila… Da kallo Alh. Sulaiman ya bisa yana wani murmushin mugunta. Shima ya kai wayarsa kunne. Bugu ɗaya Malami ya amsa da ga can. Batare da ya amsa gaisuwar Malamin ba cikin bada umarni ya furta, “Yaron dake mana aiki a gidan Isma’il Jiƙamshi ina buƙatarsa”.
“Angama ranka ya daɗe”.
Malami ya faɗa cikin tsantsar girmamawa tamkar yana a gaban ubangidan nashi ne…..
★★……
Alhaji Sufi Ado Garko da ke zaune a falonsa na baƙi har yanzun, dan bayan fitowa sallar la’asar ya sake wasu baƙin da suka sake rikita masa lissafi. Ba kowa bane face tsohon gwamna sannan babban ɗan kasuwa M Atik Kumo mahaifin MM Atik Kumo da tawagar abokansa uku neman izini wa ɗan nasa fara neman soyayyar Mawaddat. Sun gama masa bayanin kenan ya tabbatar musu da abinda ya faru game da kawo wanda Mawaddat ke so a yau har ma sun basa damar turo magabatansa suka masa godiya da bada haƙuri dan mahaifin MM Atik mutumin kirki ne. Ya fahimci bayanin Baba ya kuma gamsu suka rabu cikin girmama juna dan Baba ya kasance tamkar uba ga duk wani ɗan siyasa to. Bayan fitarsu ne yana ƙoƙarin tashi ya shiga ciki dan ya huta da hayaniyar da ya sha kiran matar ɗansa Alh. Sulaiman ya shigo masa. Bai kawo komai a ransa ba dan shi surukansa tamkar ƴaƴa suke garesa. Bayan sun gaisa tai masa barka da sauka da yaya jiki tare da bada haƙurin rashin zuwa tarbarsa saboda batajin daɗi ne. Ya gamsu da abinda ta faɗa tunda tabbas bai ganta ba a cikin gidan dan haka ya saka mata albarka. Ɗan jimm da tai ya sakashi fahimtar akwai wani abu, dan haka ya tambayeta. Sai da ta sake kwantar da murya cike da kissa ta zayyano masa dukkan abinda ƙanwarta ta tabbatar tajiyo, sai dai tace itace taji ba ƙanwar tata ba. Ta kuma kira ta faɗa ne dan kar abinda zasuyi ɗin ya taɓa kimar Baba da Family ɗin. Amma dan ALLAH bata son kowa yasan ita ta faɗa gudun abinda zaije ya dawo. Murmushi Baba ya saki irin na manya. Ya sake saka mata albarka sannan sukai sallama. Yasan Sulaiman zai aikata abinda ma yafi hakan, kuma shima yayi tunanin wani abun zai iya ɓullowa game da hukuncin nasa. Sai dai abinda ya bashi mamaki mi yake faruwane haka maneman Mawaddat ɗin keta karakaina a wannan gaɓar? Ko dai rawar data taka ne game da shari’ar mutumin nan ta kwanan nan data ɗauki hankalin mutane da yawa ce? Dan duk da baya ƙasar kunnensa da idanunsa na a Nigeria ɗin. Yafi zaton hakan shiyyasa bai ɓata lokaci wajen zurfafa tunani ba. Sai ma ya dannama Uncle Yousuf kira dan ya gama tsara kafin Sulaiman ya ƙulla abinda yake tsarawa shi zai tabbatar masa wanda ya rigaka kwana zai rigaka tashi……
★★…..
Sosai mamaki ya dabaibaye Uncle Yousuf da ke sauraren Baba. Dan ya masa bayani ne akan zuwan su M Atik Kumo kafin hukuncin da ya yanke a yanzu-yanzu saboda labarin da ya samu na shirin ɗansa da jikansa. Cikin girmamawa da godiya Uncle Yousuf ya tabbatar masa yanzu nan zai tura a isar da saƙon in sha ALLAHU. Suna yanke wayar kuwa yay kiran abokinsa Coach ɗin su Smart Abdull-Hameed, wanda ta sanadinsa ya fara sanin Smart ɗin dama. Tun yana waya da Hameed ɗin kiran Yayansa (Daddy) ke shigowa, bai ɗaga ba har sai da ya kammala da Hameed ɗin. Wani kiran ne ya sake shigo masa, ya ɗaga yana kaiwa kunne da faɗin, “Yaya irin wannan kira lafiya dai ko?”.
“Inafa lafiya Yousuf! Wai kaji suma su M Atik Kumo sunzo nemawa ɗansu izinin neman Mawaddat. Anya abunnan na lafiya ne? Ni bama wannan ya damen ba, dan M Atik mutumin kirki ne, ɗan nasa ne kawai sai a hankali, dan wlhy da ace ya kasance mutumin kirki kamar mahaifinsa da hankalina zaifi kwanciya da aura masa Mawaddat fiye da yaron nan daka kawo….”
Cikin gatse Uncle Yousuf ya ce, “To kodai a bama ɗan M Atik ɗin dama kawai, tunda shi dai ai ba wani abu ya taɓa aikata mana ba. Sannan a a bayyane ban taɓa jin ance ga aibun yaron ba…”
“No no no Yousuf bar wannan maganar kai dai. Dan wlhy ina gama waya da Baba yanzu na ɗan fara bincike kan yaron wajen wani aminina al’amarin babu daɗin ji, dan akuyace lulluɓe da fatar kura bai gado uban nasa ba. Kayi haƙuri bakwai kushe yaron nan Aliyu nake ba. A’a kawai ina tunanin taya zai iya riƙemun yarinya bashi da aikin yi, danni ban ɗauki direbanci wani abunyi ba face hanyar maƙalewa domin rage matsaloli…”
“Humm Yaya kenan. Nifa ban tsawwala ba, idan akwai wani da kake ganin hankalinka ya kwanta da shi game da Mawaddat ƙofa a buɗe take ka kawosa mu canjashi da Aliyu dan shi dama bawai ya ɗauki abun da girma bane tunda auren wata ɗaya kacal ne zai saketa, ni kuma na gaji da maimaita magana ɗaya”.
“Ina ai zancen wani ma bai taso ba auta. Yanzu fa Baba ke sanar min kuma munafukin can abinda yake ƙullawa akan ɗansa. Kaga ko ai bamu da wani isashen lokaci. Mu ƙarasa da Aliyun kawai sai dai zamuyi komai a rubuce da ƙa’idoji dan karma da ga baya wani abu saɓanin wanda akai a rubuce ya biyo baya tunda mun samu Mawaddat ɗin ta amince babu rigima. Sannan zan basu gidan da zasu zauna a kuma canja masa aiki”.
Sosai takaici yake neman shaƙure wuyan Uncle Yousuf. Amma sai ya danne ya ce, “Nima munyi waya da baban yanzu. Yanda kuma kake so haka za’ayi. Zan cema Aliyun ya tsaya idan ya kawota sai muyi maganar, idan kuma zamu bari ne sai zuwa weekend zaifi a nutse”.
“Eh weekend ɗin yayi kawai ALLAH ya kaimu”.
Sallama Uncle Yousuf yay masa tare da kashe wayar gaba ɗaya ma. Takaici yakeji na ɗan uwan nasa da halayyar da yake nunawa akan al’amurin Mawaddat mara fasali. Ya rasa wane irin soyayya yakemata irin haka. Ya kamata ace yayi nadama da neman hanyar gyara. Sai dai kash, nadamar tasa alokacin da ya ganta cikin wani hali ne kawai yake yinta…..
★★…..★
Duk wannan cakwakiya da ƙura da take cigaba da tashi a wannan yini da ga mai gayya da aiki kam normal ne. Dan tuni ta tattara komai ta watsar ta tattara hankalinta akan case ɗin yarinyar nan da akaima fyaɗe dake neman caza mata kai. Tun bayan isarsu office bata wani zauna ba ta fito suka sake fita. Kasancewar hankalinta ga a inda yake ya sa yau tsakaninta da drivern nata babu masifa. Sun ɗanyi yawace-yawace har kusan bayan sallar la’asar sannan suka koma office. A hanyar komawar ne ya fahimci ana binsu a baya. Da farko bai kawo komai a ransa ba sai da ya ga bayan ta shiga office tai zaman kusan mintina talatin ta fito zai maidata gida a hanya ya sake ganin motar ɗazun ɗin nan dai da napep a biye da su. Yaji a ransa cikin biyu dole ai ɗaya. Kodai su Honorables, ko kuma Alhajin nan da ya sa aka sace shi wancan karan a yau kuma ya ganshi a gidan Baba. Yafi buƙatar ya kaita gida lafiya daga nan koma mizai farun ya faru, dan haka ya take motar ya tsere musu cikin salon canja titi gaba ɗaya……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣1️⃣
…….Mawaddat da ke da burin amsar saƙo ta kallesa fuska babu wasa. “Malam miye na canja hanyar? Dalla ka koma tacan ina buƙatar amsar saƙo”.
Shiru kamar bazai tanka mata ba sai kuma ya bata amsa a taƙaice. “Akwai holdup ta canne, ga shi lokacin sallah ya kusa bana buƙatar rasa jam’i”.
“To ɗan iya wannan kuma matsalarka ce. Bai kuma damen ba. Ka koma ta inda nace bana buƙatar sharhi”.
Hanyar ya canja batare da ya sake cemata komai ba, amma kuma ba wadda dai take son abi ɗin ba dai ce. Dan zuciyarsa ta bashi kayan shaye-shayen nata ne zata amsa. Takaici ya turniƙe Lulu. Dama ga gajiya na nuƙurkusarta, ai tuni ta balbale sa da masifa amma yay biris da ita kamar yanda ya saba, bai ƙara tari ba har suka iso gida. Buɗe motar tai a fusace ta fito, dai-dai da shima yana fitowar da nufin buɗe matan. Ta zabga masa uwar harara da wani banzan kallo. Nunashi tai da ɗan yatsa tare da tattaro dukan ƙarfinta na zazzage masa abinda ke a ranta amma ko kalma guda ta gagara fita mata a harshe saboda yanda ya wani tsareta da idanunsa data raɗama suna irin na macizai. Sai lips ɗin ta ne kawai ke rawa kamar wanda ya ɗaureta da idanun nasa. “Kaje na koreka, da ga yau bana buƙatar sake ganin wannan shashashar fuskar taka illiterate velleger…!”
A hankali ya lumshe idanun nasa sai kuma ya sakar mata wani shegen murmushi da ya kusa fisge mata numfashi gaba ɗaya. Jitai kamar zata zube a wajan tsabar wani ƙudu dun takaici da murmushin sa ya haifar mata. Dan bata fassarashi a komai ba face na rainin wayo. Fahimtar ya samu nasarar ƙular da itan da yake buƙata ya sashi matsota a hankali, cikin ƙasa da murya da wani maidata can ƙasan maƙoshi ya furta, “Oh! Kin fison sake ganin angon naki kawai a ɗakin barcinmu ke nan AMARYA, ba damuwa a bani albashina dan da shi zan biya sadaki”.
“What!!!” ta faɗa da ƙarfi tare da kai ma fuskarsa mari da gaba ɗaya ɗan sauran ƙarfin da ya rage mata a jiki. Baya yay cikin wani salon da ta samu iska shuuu, ya ɗago yana murmushi tare da kashe mata ido ɗaya, sai kuma ya nuna fuskar tasa da yatsa yana ɗan sake matsota harda ranƙwafowa kaɗan. “Duk randa wannan hannun ya sauka kan wannan fuskar da sunan mari to kisa a ranki MAZA sun faɗi, faɗuwa irin ta MUTUWA. dan itace kawai damar da ƘYANWA zata iya samun yin birgima a gaban ZAKI yanda take so”. Ya ƙara kashe mata ido ɗaya yana ɗaga mata yatsu biyu da faɗin, “Bye *MATAR ILLITERATE*”. Yay gaba abinsa.
Yuuuuu!! Lulu ta dinga jin hajijiya na neman kwasarta, wato itace ma ƙyanwar yake nufi. Dariya sosai Uncle Yousuf da ke cikin motar dake a kusa da su batare da sun san akwai mutum a ciki ba ke tuntsurawa harda ƙwalla. Ashe zaton da yakema yaron nan ya wuce nan. Kai jama’a har ya fara tausayin ƴar tasa gaskiya. Dan tabbas akwai babban wasa a wannan tafiya yanzu ne kuma za’a fara. Ganin yanda ta wuce tana haɗa hanya ga hawaye sun wanke mata fuska ya sashi daina dariyar ya buɗe motar ya fito, sai dai duk yanda yake son binta ya haƙura dan lokacin sallah yayi. Ya kai dubansa ga su Smart da ke alwala sai kawai ya nufesu yana gyara yanayinsa kamar bashi ya gama kwasar dariya ba a mota…
Bayan an idar da salla kusan a tare suka fito. Uncle Yousuf ya dakatar da Smart da ke sallama da su maigadi akan ya jira su wuce tare. Kamar zai ce a’a sai kuma dai yay shiru dan kiran da Abba yay masa suna ƙoƙarin shiga massalaci akan idan ya dawo gida ya sameshi falonsa yanzun nan. Yasan maganace da Abban, shi kuma da yayi niyyar bama masu bin san nan a baya dama dan ya tabbatar ba haƙura sukai ba su kamashi dan yana son yin magana da koma waye ya turosun. Babu yanda ya iya dole yabi Uncle Yousuf ɗin, shiko ya ƙaunaci ALLAH ya kaisa har gida yau. Tunda suka fito kuma yaga motar nan sai dai ba napep ɗin yanzu, motar dai ce ke cigaba da binsu yanzu ma. Suna isowa titin anguwarsu yaga sun dakata cikin takaici direban motar na kaina sitiyari duka alamar ba haka sukaso ba. Sai dai kuma abinda bai sani ba shima Uncle Yousuf ya san da su shiyyasa ma ya ɗakkosa ya kawo har gidan.
“Alhaji yau na saka ka aiki, Nagode sosai”.
Murmushi Uncle Yousuf da idonsa ke kan mirror yana kallon mutanen nan ya saki, tare da faɗin, “Har yanzu dai ina a Alhaji na? A tunani na na zama Uncle yanzu tunda ƴa zan bayar duk da auren wucin gadi ne”. Yanda Uncle Yousuf ɗin ya ƙare maganar ne ya saka Smart kallonsa, sai kuma ya ɗauke kansa yana sakin murmushi ya ce, “To ayi haƙuri Uncle”.
“Shike nan na haƙura, dan dama ba’a san iyaye da fushi da ƴaƴansu ba. Ina fatan zaka samu Abba da maganar yau ko?”.
“Da wuri haka?”.
Smart ya faɗa da mamaki yana kallon Uncle Yousuf ɗin.
“Dole ne muyi da wurin, dan ɗazun Baba ya sake kirana akan zuwan M Atik Kumo shima yana nemawa ɗansa aurenta, sannan Alhaji Sulaiman da ɗansa sun gama ƙulla matakin da zasu ɗauka a gobe idan ALLAH ya kaimu…..” tsaf ya zayyane masa komai shima. Mamaki ne ya sake lulluɓe Smart, yayinda a ƙasan zuciyarsa yake ta lissafi akan yanda zai canja salon wasan a yanzu tsakaninsa da Alh. Sulaiman. Kafin yanzu shi bai wani ɗauki zancen da muhimmanci ba, dan har ya gama ƙulla yanda zai kuɓuce wa al’amarin, sai dai a yanzun nan ya canja sabuwar shawara. Duk da bai san minene dalilin Alh. Sulaiman ɗin ba ya kamata ace ya nuna masa shima tsageran kansa ne a wannan gaɓar. Bai damu da zancen MM Atik Kumo ba…..
“Aliyu kayi shiru!”
Uncle Yousuf ya katse masa tunani. Iska ya ɗan furzar kaɗan sai kuma ya fuskanci Uncle Yousuf ɗin. Cikin sake furzar da wata iskar ya ce, “ Please Uncle kozan iya sanin yaya kuke da shi Alh. Sulaiman ɗin?”.
“Yerh babu damuwa Aliyu. Alh. Sulaiman Sufi Ado Garko ɗane ga Alhaji Sufi Ado Garko. Sannan Yaya ga mahaifiyar Mawaddat uwa ɗaya uba ɗaya. A shekarun baya ɗan uwana mahaifin Mawaddat abokai ne da Alh. Sulaiman na ƙut-da-ƙut, dan sun haɗu ne tunkan ya auri mahaifiyar Mawaddat ɗin adalilin shi Baba da ya ja Yayana jikinsa. Sai dai a yanzu ba haka bane, dan bamu san minene ya shiga tsakanin wannan amintaka ba abokan biyu suka zama maƙiyan juna ta yanda ko inuwa ɗaya basa sha. Iya tambaya na yima Yaya amma yaƙi faɗa min komai. Shi iyakarsa fita harkar Sulaiman, amma shi Sulaiman a bayyane yake nuna tsanarsa garesa da mu ma ahalinsa gaba ɗaya shiyyasa Yayana yay ruwa yay tsaki wajen hana aure tsakanin Tajuddeen da Mawaddat dan yace akwai manufa. Wannan shine iya abinda na sani gaskiya”.
Kai Smart yake jinjina wa cike da gamsuwa. Sai da Uncle Yousuf yay shiru sannan shima ya bashi labarin kamasan da Alh. Sulaiman ɗin yayi a randa yazo shi da Ahmad suka roƙesa ya koma aiki, ya kuma sanar masa aikin da yace ya koma yay masa tare da nuna masa motar yaran Alh. Sulaiman da ke tsaye a bakin layinsu kasancewar suna iya hango su da ga nan ƙofar gidan su Smart ɗin da ke a bakin titin.”
Sosai al’amarin ya girgiza Uncle Yousuf ɗin, ya kuma tabbatar masa da shima dalilinsa na kawoshi gida yanzun. Dan tunda suka kammala waya da Baba yaji a ranasa Alh. Sulaiman zai iya ɗaukar mataki kowane iri ne akan Smart shine ya saka wani ɗan sanda zuwa office ɗin Lulu ya saka masa ido, ɗan sandan ne ma a Napep ashe, sai ko gashi bayan tahowarsu gida ɗan sandan ya tabbatar masa ana binsu… “Wato Aliyu idan na fahimta tun fara aikinka da mu Alh. Sulaiman na biye da lamarinka kenan? Kuma bana raba ɗayan biyu a wajen Tajuddeen ya sani. Lallai ya kamata musan dalilinsa danni zuwa yanzu har Tajuddeen ɗin ma na saka masa alamar tambaya”.
“Sanin dalilinsa abunne mai sauƙi Alhaji, yanzu dai barshi na fara masa duka a ciki, bayan cikin ya ƙulle zai amayar da duk abinda ke a ransa da kansa. Sannan Tajuddeen bai zama lallai yasan komai ba, zata iya yiwuwa amfani uban keyi da shi batare da shi ma ya sani ba”.
Murmushi Uncle Yousuf yayi tare da bubbuga kafaɗar Smart, dan tsaf ya fahimci inda zaurancen nasa ya nufa game da duka a ciki. Murmushi shima Uncle Smart ɗin yayi tare da buɗe motar yay masa godiya ya shige gida, shi kuma yaja motar yana ƙara jin ƙaunar yaron har tsakkiyar ransa. A rayuwa yana matuƙar ƙauna da son jarumin mutum. Musamman ma matashi irin Smart mai tsayyar zuciya. Wannan nagartar tasa ya fara hanga a filin ƙwallo ya shige masa zuciya, faruwar ƙaddarar data nema dakushesa da ga cikar burinsa ta fara sakashi jin tausayinsa da laluben hanyar da zai iya taimaka masa. Bayan yin dogon nazari ya yanke shawarar kusantosa gefensa domin ƙara tabbatar da halayensa kafin ya ja hannunsa hanyar da ya gama shiryawa domin kaisa ga cikar burin nasa. Sai kuma ga al’amarin ƴar ɗan uwansa ya gitta a cikin labarin tamkar bakangizo a tsakiyyar gagarumin hadarin da ke gab da zubda ruwa. Fatansa kawai ta kasance bakangizo mai amayar da ruwan da ta shanye bamai haɗiyewa ba har abada………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣2️⃣
…….Bai samu ganawa da Abba ba sai bayan sallar isha’i ya samesa a falonsa. Bayan sun gaisa cikin dakewa Abban ya ce, “Aliy!”.
Ya amsa da “Na’am Abba”.
“Aliy!”
Ya sake ambata. Shima sake amsa masan yayi kamar farko. Malam Mika’il bai gajiya ba ya sake kiransa a karo na uku shi kuma ya amsa masan dai kamar yanda yay na farko da na biyu.
“Na kiraka sau uku ko?”.
Kai ya gyaɗa masa alamar eh.
“Na kiraka badan tisa maka sunan da ni na saka maka ba ne, na kiraka ne domin a yau zan tabbatar maka da magana ta ƙarshe ne akan aurenka. Dan duk maganganun da Yahanasu ta faɗa ɗazun akanka sun sosama mahaifiyar ka da nima kaina zuciya. Kuma mun ɗauki alƙawarin bazaka sake rufa wata anan gidan babu matar aure ba. Dan haka a yanzu ina son jin ta bakinka, idan kana da wadda kake so sai ka faɗeta, idan kuma babu mahaifiyarka ta maka mata, nima kuma na maka sai ka zaɓi guda a ciki.”
Sai da ya ɗan rumtse idanunsa da jan numfashi, sannan ya ɗago a hankali ya kalli mahaifin nasa. Sai kuma ya sake maida kansa ya duƙar. “Kuyi haƙuri Abba duk ni ne na ja muku, amma insha ALLAH komai yazo ƙarshe, ba sai kun nemomin mata ba ni da kaina ma na samota”.
Wata irin ajiyar zuciya Abba ya sauke a hankali, sai dai cikin dakewar san nan ya ce, “Wacece? Ƴar wanene? A ina kuma ta ke?”.
Duk da yawan tambayoyin bai gazaba wajen amsasu ga mahaifin nasa. Ya ce, “Yarinyar da nake aiki gidansu. Ɗiya ga Alhaji Isma’il Jiƙamshi. A yau suma kuma suka buƙaci na turo iyayena dama in har na shirya”.
“Alhamdullahi. Aliyu Hydar ka daɗe baka faranta min rai irin yau ba. ALLAH yay maka albarka. Ya yaye maka dukkan damuwarka. Ya ɗauraka akan maƙiyanka. Ya kawo maka mafita ga al’amuranka. Na amshi zaɓinka badan ta kasance ɗiyar Alhaji Isma’il Jiƙamshi ba, ko dan yana da kuɗi, sai dai dan nasan kai nagartaccen mutum ne da bazai taba yin zaɓen tumun dare ba.”
(Abba ka gafarceni wannan dai kam zaɓen tumun asubace ma ƙarewar dare) ya faɗa a zuciyarsa. A zahiri kam murmushi kawai yayi da faɗin, “Nagode Abba. ALLAH ya ƙara lafiya da nisan kwana mai amfani. Ku gafarceni akan dukkan abinda nai muku ba dai-dai ba kuma insha ALLAHU zan cigaba da zama a fiye da yanda kuke buƙata”.
Sosai Abba yay murmushin jin daɗi, Aliyu na cikin ƴaƴan da yafi ƙauna a cikin ƴaƴansa, sai dai shi kansa a wasu lokutan bai san mike danne soyayyar ba yayta kyararsa da hantararsa a dalilin ƙaddarar da wani bai isa ya canjata ba. Albarka sosai ya saka masa sannan ya sallamesa. Koda yabar wajen Abba cikin gida ya shiga, sai dai kai tsaye ɗakin Ammah ya shige yau bai gaida kowa ba a matan gidan. Ya samu tana shirin fitowa kaima Abba abinci dan yau itace da shi. Ya fahimci tana cikin damuwar da ya san babu makawa akan abinda ya faru ɗazune tsakaninta da Umma. Ƙannensa kansu yau basa cikin walwala. Suna gama gaisawa Ammah ta fice, annan ne Hawwah ke bashi labarin faɗan da akai sosai ne ai yau ɗin kuma duk a sanadinta ne. Da ga ƙarshe aka ƙare da musu goron halin da yake a ciki. Sosai ya ƙara jin zuciyarsa ta Zafafa. Sai dai komai bai ce ba yay musu sallama ya tafi makwancinsa……
*_WASHE GARI_*
Washe gari batare da sanin kowa ba Abba da tawagarsa suka nufi gidan Alhaji Isma’il Jiƙamshi nemawa Aliyu Hydar auren Mawaddat Isma’il Jiƙamshi. Sun sami tarba ta mutunci dan har Baba ma yazo gidan shima. Abinda zai birgeka babu ƙyama ko hantara irin ta mai kuɗi ga talakawansa. Abin farin ciki da mamaki ashema Alh. Sufi Ado Garko school mate ɗin Abba ne ma a secondary school. A take hira ta kaure a tsakaninsu har zuwa kan abinda ya tarasu. Sai dai kuma bayanin da shi Baba yazo da shi ya girgiza su a wajen. Dan a ganinsu babu wani shiri ai tare da su game da haka. Baba ya kwantar musu da hankali tare da tabbatar musu da dalilansa masu ƙwarin gaske ta yanda su duka suka gamsu da hakan. Sun ɗan ƙara tattaunawa sannan sukai musu sallama cike da jin daɗin karramawar da suka samu suka suka taho akan sai anjima idan sun haɗu ɗin….
★★……
Sam Smart bai san mima ake ciki ba. Dan hatta zuwan nasu Abba bai san da shi ba saboda yau bai ma fita aiki ba. Tunda ita tace ta koresa da kanta a ganinsa babu amfanin ya koma su sake raba hali. Dan haka ya zaɓi yin kwanciyarsa a ɗaki yayta buga game ɗinsa hankali kwance har lokacin sallar juma’a ya gabato. Yana shirin shiga wanka Ahmad yazo gidan. Zuwan Ahmad gidan ba sabon abu bane garesa dan haka bai damu ba. Haka koda ya bashi shadda sabuwa fil yace ita zai saka bai kawo komai a ransa ba dan Ahmad ɗin ya sha musu ɗinki irin hakan, haka shima kansa yasha yi musu ɗinki a taren.
Bai wani ɓata lokaci ba ya fito a wankan, Ahmad na zaune har ya kammala shirinsa. Yayi ƙyau matuƙa kamar ka sacesa ka gudu. Ahmad ya wani shiga masa ruwan turare. Warce turaren Smart yay yana hararsa da faɗin, “Kaifa a duniya kamar baka san wahalar kayan duniyar nan ba. Anata wannan yanayin zaka ƙaramin turare haka dan neman hanyar talautani”.
Dariya kawai Ahmad yay masa da kashe ido ɗaya ya furta “Am sorry Zakin zaki”.
Shima dariyar yay a karo na farko. Dan duk sanda ya kira shi da Zakin zaki yana nufin shi ɗin na Coach Hameed kenan yayansa. Cikin nishaɗi da farin cikin tsokanar juna da suke na kiran tuzurai suka fita. Jan Ahmad yay suka shiga ciki gaida Ammah. Ta saka masu albarka tare da addu’a data so tsayama Smart a rai. Amma sai ya danne ta a ƙasan rai da tunanin Ammah tayi addu’ar ne kawai domin gabansa. Daga haka suka taso suka fita acewarsu zasuje sallar juma’a su dawo nan suci biranuskon da Amma keyi matsayin abincin rana…
“Wai wane massalaci zaka akaimu haka ne?”.
Cewar Smart yana kallon Ahmad dake drivering a nutse. Murmushi Ahmad yay masa idonsa a titi ya bashi amsa da “Mi kakeci na baka na zuba? Zaka gani ai”. Baki Smart ya ɗan taɓe da cigaba da game ɗinsa a waya. A haka suka cigaba da ƴar hirarsu har suka iso massalacin juma’ar. Zamansu babu jimawa aka fara khuɗuba, dan haka suka nutsu wajen saurare har aka kammala. Ana ƙoƙarin tada salla ya hango Uncle Yousuf da Coach da ke isowa yanzu, da alama sun makara ne. Baice komai ba ya gyara tsaiwarsa aka tada salla. Kasancewar bayan idar da sallar juma’a yin ɗaure-ɗauren aure a massalacin normal ne yasa bai kawo komai a ransa ba. Sai dai haka kawai yake jin sa wani iri yau kamar wani abu na shirin faruwa da shi. Ga kansa da ke ciwo ƙasa-ƙasa amma dai sai ya daure tunda bawai ya matsa masa da yawa bane. Wani irin harbawa da dokawar ƙirji ce ta samesa a lokaci guda a dalilin jin sunansa matsayin angon da aka ɗaurama aure da amarya mai suna Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. Shi al’ajabi ne ma ko ruɗani yama rasa ganewa. Ya dubi Ahmad da ke kallonsa yana dariya, “Kai nifa ban ganeba wlhy, wai waye haka mai irin sunana komai da komai fa”.
Sake tuntsirewa da dariya Ahmad yayi har da riƙe ciki. Sai da yaga Smart ya turɓune fuska har yana harararsa sannan ya ɗan sassauta. Sai dai maimakon amsa masa sai ya miƙe dan yau dama ɗaurin auren biyu ne kawai ma, bayan an ɗaura na farko da ya kasance Smart da Lulu na biyun kuma aka fahimci shima dai da amaryar farko ne da wani angon, dan kuwa dai Alh. Sulaiman ne ya ƙulla, abin mamaki kuma babu shi a massalacin sai Tajuddeen kawai da gayyar abokansa. Yana jin kuma an ɗaura auren Lulu da Smart ya yanke jiki a wajen ya faɗi. Su dai mutane basu fahimci minene matsalar ba, haka ma su Abba magabatan Smart dan sai da aka tashi idonsa ya gane masa mahaifin nasa da tawagar dattijan anguwarsu. Sagade kawai yay yana kallonsu kamar television. Abba da ke kallonsa da murmushi ya ce, “Ɗan nema daina kallona ni, ko duk murnar ce ta saka sumar tsaye”.
Dariya dattijan suka sanya har da Baba. Uncle Yousuf da ke jin ALLAH ya gama masa komai a yau ya matso ya kama hannun Smart cikin nasa ya jasa ya rungume. “FATAN ALKAIRI SURUKINA”. ya faɗa cikin kunnensa. Kamar wanda aka farkar a barci Smart ya ja nannauyar ajiyar zuciya. Cikin marairaice fuska alamar yaya haka.. yake kallon Uncle Yousuf. Shiko ya sake faɗaɗa dariyarsa da ɗan ɗage kafaɗa alamar nima ban sani ba. Coach ma rungumesa yayi yana mai jera masa addu’oi. Shi gaba ɗaya ma ya kasa iya furta komai. Sai da Ahmad yaja hannunsa gaban su Baba sannan ya motsa gaɓɓansa da ƙyar. Rissinawa sukai suka gaida Baba da ke zagaye da manyan mutane ciki harda gwamna. Abin zai baka mamakin yanda har aka iya haɗa mutanen bayan auren babu wani shiri a cikinsa. Koda yake ba abin mamaki bane idan akai dubi da girman Alh. Sufi Garko ɗin da ƙarfin ikon da yake da shi wajen manyan jihar. Sosai manyan mutanen nan suka dinga saka masa albarka kowa na jansa jiki ganin yanda Baba ya damƙe hannunsa cikin nashi shima. Daddy ma sun gaisa yana ƴar fara’arsa dai. Daga haka suka ringuɗa zuwa government house. Dan sakamako gwamna ne ya bada auren Mawaddat matsayin waliyyi yasa shi shirya liyafar cin abinci bayan ɗaurin auren. Smart dai ya zama kamar wani butun butumi. Komai ɗaukarsa yake kamar a mafarki. Ga kansa dake ƙara nauyi matuƙa har idanunsa na ɗan rinjayar ganinsa. Amma dai yanata dakewa kodan fidda mahaifinsa kunya. Dan duk da Malam Mika’il Idris Mawashi ba mai tarin dukiya bane. Dattijo ne nagartacce mai cikar kamalar da masu kuɗun dole suga girmansa da jin shakkar kawo masa raini. Shi da kansa ya biyama ɗansa sadaki naira dubu ɗari biyu. Sai dai Baba ya ce ɗari kawai zasu amsa ALLAH ya sanya albarka. Hakan ya ƙara sakama Abba jin kimar mutanen. Dan shi mutum ne mai girmama mutumtaka fiye da dukiya. A Government house mutanen da suka taru har sunfi na massalacin yawa saboda wasu sun iso a makare sai dai walimar zasu samu kasancewar sakon gayyatar ɗaurin auren yazo musu a ƙurarren lokaci dan a jiya jiyan nan da dare duk Baba yasa aka watsa shi a waya ta hanyar contacts ɗinsa dana Uncle Yousuf da na Daddy. Amma da ace shirine na musamman ai sai ma an rasa masaka tsinke. Sai dai hakan ma Alhamdullah, dan basuyi zaton taruwar mutanen kamar hakan ba amma sai gashi kamar wasa a kaso uku da suka gayyata kaso kusan biyu sun halarta bayan wanda sukaje massalacin salla kawai. Anci ansha anyi asuwaki da kaji yanda ya kamata, sai dai ango ya gagara cin komai. Ga abokansa ko nace teammate ɗinsa na ball zagaye da shi sunata masa shaƙiyanci da masa ciwon bakin jin auren a ƙurarren lokaci da sukai. Haka dai yayta daurewa har aka kammala cin abinci aka shiga hotuna. Nanma dauriyar yay tayi kasancewar duk wanda zai ɗauki hoto sai an jajubosa musamman ma manyan mutanen nan da ke nanuƙe da Alh. Sufi Garko. Shigowar lokacin sallar la’asar ne yay belinsa. Da ga salla kuma kowa zai kama gabansa……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣3️⃣
……Sam Lulu bata san wace waina ake toyawa ba. Dan yau ma dai tashi tai da ciwon kai har da zazzaɓi sakamakon mura da ta mata ɗaurin kazar kuku. Da ƙyar ta iya tashi kusan 12 da Mommy ta tasheta akan tai wanka. A sannan ne ma suka san bata da lafiyar. Bayan ta ɗan samu tai wankan ne ta sha tea da Mommy ta haɗa mata da kanta mai kayan ƙamshi sosai. Wani irin faɗuwar gaba takeji ga rashin lafiyar da ta kadata. Da ƙyar ta samu ta ɗanyi waya da Zainab dan jin yaya ake ciki a office, sai kuma Sha’aibu ɗan sanda da yay kiranta yay mata albishir ɗin cafke mijin matar nan da suka sami nasarar yi. Hakan ya ɗan faranta mata rai da jin zazzaɓin nata ma ya sauka har ta fito falo. Anan taci karo da yayunsu su Twins sun zo. Sama-sama sukai gaisuwa ita da su dan sam babu jituwa tsakaninsu. Fasa zaman falon tai ta juya ta koma ciki ranta na ƙara dagulewa. Ta rasa mitai ma ƴan uwan nata suke jin zafinta irin haka. Hira da ta samu sunayi da sauran ƙannensu har da dariya, amma ita tana fita duk suka gimtse fuska sai Suhaib da Nazeer ne suka gaisheta, sai kuma Amrah da tai mata yaya jiki. Wannan abun ya jima yana damunta, sai dai rashin riƙe abu a rai kansa ta watsar ta cigaba da al’amarin ta musamman idan tasha wani abu haka. Gadonta ta koma ta kwanta dan da jikinta yay mugun zafin zazzaɓi, barci ne mai nauyi ya ɗauketa batare data shirya hakan ba. Hakan yasa har su Abba suka fita massalaci tare da yayunta da Mubeen da su Suhaib bata sani ba. Ba kuma ta farka ba har bayan la’asar da ƴar hayaniyar da gidan ya ɗauka ya farkar da ita da ga barcin da take mai cike da mafarkin mahaifiyarta da take matuƙar bege, sai drivern ta da bata san daga ina kuma mafarkin nata ya yayo mata shi ba dan ita dai bata kwanta da tunanin ko mai kama da shi ba balle ace. A hankali ta ɗan ja tsaki da murza goshinta da yay mata nauyi. Zazzaɓin nata ya sauka, sai dai nauyin da kan nata yay mata da rashin jin ƙwarin jiki. Landline phone da ke saman bed side drawer ɗinta ta ɗauka tai kiran sashen masu aikin gidan. Batare da jiran jin waye ya ɗauka ba balle amsa sallamarsa tai umarnin ganin Iya Tabawa ta yanke wayar ta ajiye. Cikin mintuna kaɗan kuwa sai ga iya Tabawa na faman washare baki. Kallo ɗaya tai mata ta ɗauke kanta cikin bada umarni kamar yanda ta saba ta ce ta haɗa mata ruwan wanka.
“An gama ranki ya daɗe”. Iya Tabawa ta faɗa tana nufar bathroom cike da farin cikin abinda su Daddy suka shigo da shi gidan cewar an ɗaurama Lulu aure. Harga ALLAH da gasken gaske son yarinyar take da ƙaunarta. Duk halayyar Lulu a gidan ta taka ma’aikata baisa taji ƙinta ba. Dan duk wulaƙancin da take musu hakan bai hanata ƙyautata musu randa ta so ba kuma musamman ma ita. Ba kuma komai ya ƙara girmama farin cikin ta ba sai jin wanda Lulun ta aura, dan ita sam bataga hakan komai ba duk da sauran ma’aikatan gidan na can na dariya da gulmar wai alhakinsu ne ya kamata ta ƙare da auren drivern ta. Dan su sosai abin yay musu suga da kallon cewar Lulu tayi faɗuwar baƙar tasa. Tana ƙoƙarin shiga wankan ta bama Iya Tabawan umarnin haɗa mata farfesun kifi mai yaji sosai dan Lulu na matuƙar son kifi a rayuwarta. Harta nufi ƙofar fita Lulun ta dakatar da ita.
“Wai lafiya ne a gidan aka ishi mutane da hayaniya? Kema naga sai wani washare baki kike”.
Iya Tabawa da murmushi ya kasa barin fuskar tata ta ce, “Muma dai bamu san mike faruwa ba Aunty, munga dai su Alhaji ƙarami (Uncle Yousuf) nata farin ciki inagama aure dai ya ƙara”.
“What?! Uncle You ɗin ne ya ƙara aure ki kike nufi?”.
“Bani da tabbacin hakan Aunty, hasashen dai kawai nake”.
Tsaki Lulu taja cikin taɓe baki ta nufi bathroom ɗin cikin ƙunƙuni take faɗin, “Kai wannan tsohuwa da neman masifa kike. Haka kawai da ranar nan tsaka ace amma Aunty Saliha kishiya ai akwai ƙura. Dan koni nan na korar mata shegiya”. Daga haka ta shige.
Ta fito a wankan tana cikin shiryawa da kaya marasa nauyi na wando da riga akai mata knocking ƙofa. “Waye?” ta faɗa tana fesa turarrukanta. Uncle Yousuf ya amsa mata da cewar shine. Ƙofar ta nufa da sauri tana faɗin, “Uncle You!”. Amsa mata yay yana turo ƙofar ya shigo, dan haka suka kusa cin karo. Baya taja da sauri tana mai zuba masa ido. Cikin kasa danne abinda ke bakinta ta ɗan waro manyan idanunta ta da faɗin, “Oh god wai da gaske ne kenan?”.
“Da gaske mi?”.
Ya faɗa idonsa a kanta. Fuska ta ƙwaɓe da wani yamutseta. “Kishiyar kaima aunty Salihar mu Uncle?”. Yanda tai tambayar da wani tsuke masa fuska taso bashi dariya. Amma sai ya dake ya ce, “Eh haramunne?”.
“Kutt! Wai da gaske ne ma?”.
Kasa jurewa yay yanzu kam sai da ya dara. Dan a masifaffiyarta ta sake tambayar. Ya ce, “Kinga maida wuƙar Daughter ba haka bane. Ai auntynku ita da kishiya sai a aljanna”.
“Oh har na samu relief”.
Ƴar dariya yayi yana kaiwa zaune a kan sofa. Ya nuna mata wajen zama itama. “Kinga zauna bani da lokaci magana nazo muyi.”. ganin yanda yaci serious ya sata kaiwa zaunen cikin bashi dukkan attention nata. Shima sake gyara yanayinsa yay da nutsuwarsa ya ce, “Mawaddat!”.
“Yes Papa”.
Ta amsa cikin sake nutsuwa. Cigaba yay da faɗin, “Kin san daga ina muke?”.
“Massallaci”.
Murmushi yayi da jin jina mata kai. “Yes daga massalaci muke, sai dai bayan yin sallar juma’a an ɗaura aure. Auren kuma bana kowa bane sai naki”.
Wani shegen dariya ta saki a lalace. Tace, “Uncle You ALLAH ka iya tsokana, sai kace wata babyn roba ”.
Murmushinsa ya sake faɗaɗawa da gyara zamansa. “Mawaddat ba wasa nake ba. Kema kuma kin san bana miki kalar wannan wasar ai”.
A take fara”ar fuskarta ta ɓace ɓat gaba ɗaya. Ta tsirama Uncle Yousuf ɗin ido kamar wadda tai suman wucin gadi. Fahimtar yanayin data shigan ne ya sakasa riƙo hanunta a cikin nashi yana girgiza mata kansa. “Kinga calm down sweet heart. Wannan aure ya tafi ne kamar yanda muka tsara da ke. Abinda yasa kuma akayisa yanzu ba tare da saninki ba kema shine a jiya da yamma……” ya kwashe komai game da ƙudirin su Tajuddeen da mahaifinsa ya sanar mata. Ya ɗora da hukunci baba dama abinda ya faru yau a massalaci yanzu haka ma Tajuddeen na asibiti an kwasheshi.”
A hankali ta lumshe idanunta. Sai kuma ta koma jikin kujera ta lafe dan ƙirjinta wani irin bugawa yake da sauri-sauri. Da’ace ta iya addu’a ita ya kamata ace ta karanto a wannan halin, sai dai kash hakan bai samu ba. Taja wasu mintuna a haka kafin Uncle Yousuf ya dawo da ita a hankalinta.
“Mawaddat Please relax. A yanzu haka fa tare muke da Baba a gidan nan. Kuma son ganinki sukeyi. Ina so. Ki nutsu kisa hankalinki waje ɗaya dan kar kije ki canja abinda muka tsara kuma ta ƙwaɓe, dan idan Baba ya fahimci shirinmu bake ba hatta ni da Yaya da bai san komai ba sai ranmu ya ɓaci. Ki dake zuciyarki ki nuna jin daɗinki ga hukuncinsa ta haka ne kawai zai kauda kai akan ki mu samu cikar burinmu dan zuwa dare zan nemo Aliyu yazo ayi komai a rubuce ma”.
“Uncle karfa ya bamu matsala. Wlhy guy ɗin nan yanada taurin kan masifa fiye da yanda kake tsammaninsa”.
“Karki damu insha ALLAHU babu abinda zai faru. Komai bazai canja ba da ga yanda muka tsara in har kin yi abinda ya dace yanzu a gaban Baba ta yanda bazai fahimci komai ba”.
Kanta ta jinjina masa muryarta a shaƙe ta ce, “Shikenan zanyi yanda kace. Amma Please bana son ganinsa yau sam”.
Murmushi Uncle Yousuf yayi yana miƙewa. “Baki da matsala da hakan tashi kisa mayafi muje. Koma dai ki canja kayan nan zuwa atamfa haka ki lass ok”.
Badan taso hakan ba ta gyaɗa masa kai kawai. Ya fita yana sake jadadda mata ta kiyaye dai ta kuma kula kar wanda ya fahimci halin da suke a ciki……
★…..
A ɓangaren Smart kam tunda suka bar government house hannunsa riƙe yake da kansa. Tun su Ahmad na masa shaƙiyanci da wasu a cikin teammate ɗinsa da suka biyosu a motar Ahmad ɗin har suka fahimci shirun nashi bana lafiya bane. Dan duk da dama shi bamai yawan magana bane koyaya ne zai musu murmushi ko yace wani abu koda sau ɗaya ne, balle wannan ranar a gareshi ta musamman ce, tunda su dai basu san komai game da auren ba.
“Mawashi lafiya dai?”.
Cewar Ahmad yana gangarawa layin anguwar su Smart ɗin. Kansa ya nuna masa da hannu kawai. “Subahanallahi ciwo yake maka kan?”. Kan ya sake gyaɗa masa. Shiru motar tai na ɗan lokaci duk suna kallonsa, sai kuma suka shiga jera masa. Kusan tare motar tasu ta tsaya da ta su Abba suma. Dan haka suka firfito a tare, dole ya sake daurewa dan a cikin ƙanƙanin lokaci ƙofar gidan shima ya fara tara mutane ƴan taya murna, dan al’amarin kamar busa usur zancen auren ya dinga shiga kunnuwan mutane, dama gashi juma’a ce yawancin mutane duk sun dawo gida……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣4️⃣
……..Gayyar yayunsa da ƙanne su Salim da sai da sukaje wajen ɗaurin aure suka san dawa aka ɗaura kusan ransu duk a ɓace yake, dan gani suke kamar Abban ya rufe zancen ne dan yafi son Hydar ɗin a gidan kamar yanda iyayensu kan faɗa. Komai ya sake tsaya musu a rai jin ƴar wanda ya aura da kuma Gwamna da yay waliccin auren. Zuwa walimar cin abincin ma a gidan gwamnati sai da Abba ya nuna ma wasun su ɓacin rai sukaje. Su dai su Mubarak ƙanana ko’a jikinsu, sai ma farin ciki suke ballema yau gasu a cikin government house. Sune suka fara isa gida da labarin wannan aure na bazata, dan sun riga su Abban tahowa, sune kuma suka baza batun auren a anguwar.. Smart yayi dauriyar tsayawa amsa gaisuwar mutane da taya murna kafin su shiga ciki. Sun tadda gidan a ɗan harmutse, dan kamar kowa jiran shigowar Abba yake. Shiko Abba da yasan da hakan a tsumensa ya shigo, dan haka dole kowa ta kama kanta sai dai ƴar ƙus-ƙus a ɗaki tare da yaransu dan har na ma’auri matan yau suna gida kasancewar hakan kamar ɗabi’ar yaran gidan ce duk juma’ar ƙarshen wata anan suke yini su da gayyar ƴaƴansu..
Umarni Abba ya bama Smart ya biyoshi falonsa. Ya kuma aika Musaddiq tattaro sauran jama’ar gidan suma. Cikin ƙanƙanin lokaci kowa ya hallara har falon na neman musu kaɗan. Dan kuwa dai ALLAH ya azurta malam Mika’il Idris Mawashi da baiwar ƴaƴa. Matan ne suka shiga gaisheshi da sannu da dawowa dan sanda wasunsu suka iso shi ya fita. Ya amsa musu da tambayarsu mazajensu dama yaran duk da yasan sukam duk suna tare da su anan. Zakuma su zo gaisheshi. Duk da ran wasun su a dagule yake haka suka dinga amsawa mahaifin nasu kamar yanda suka saba. Shima ya lura da yanayin wasun su ɗin, amma sai bai damuba dan yasan iyayensu mata ne suka gama kunnosu, ya kuma san bai wuce akan wannan aure na Hydar da ya sirrinta ba. Yayi gyaran murya da sake tsare gida yana maida kallonsa ga matan nashi duka huɗu.
“Zan fara da ku matsayinku na iyaye. Alhamdullah da farko zan fara da sanar muku yau dai ALLAH yayi an ɗaurama Aliy aure. Nasan abin zai iya zama abin mamaki a gareku har ma da ka-ce-na-ce. To bazan hana hakan ba, sai dai zan fahimtar da ku muma a haka al’amarin yazo mana. Ga mahaifiyar sa nan ita kanta sai a safiyar yau na sanar mata cewar zamu kai kuɗin auren Aliy domin iyayen yarinyar da yake so ɗin sun buƙaci haka sakamakon ɗan rikici da abokan neman auren nasa suke son kawo wa a ciki. Ni kaina kuma a yau ɗin munje ne da batun kai kuɗin aure sai suka buƙaci kawai a ɗaura domin hakan ya zama masalaha ya kuma bama kowa kwanciyar hankali. Sosai hakan yamun daɗi, dan ganin auren Aliy a yanzu yana ɗaya da ga cikin abinda ke damuna, bayan mun dawo naso zaunar da ku na muku bayanin halin da ake ciki sai ya zam guri ya ƙure, dan haka nace bari mu bari har sai mun dawo. To Alhamdullah yanzu dai ta ƙare, shima Aliy ya shiga sahun ƴan uwansa, sai muyi masa fatan alkairi da zaman lafiya da zuri’a mai albarka kamar saura, an ɗaura aure ne kawai sai zuwa wani satin insha ALLAHU za’ai biki duk da mu hakan dai yazo mana a ƙure amma ALLAH muka riƙe mun san kuma bazai bamu kunya ba….”
“Tofa bazawara ce kenan?”.
Cewar Umma a gatsine. Murmushi Abba yay da kafeta da idanu, sai kuma ya janye yana jinjina kansa. “Yarinya ce budurwa ba bazawara ba, ɗiya ce ga Alhaji Isma’il Ibrahim Jiƙamshi, sannan jika ga Alhaji Sufi Ado Garko”.
Kusan duk falon musamman matan babu wanda bai zabura da jin sunayen guda biyu ba. Dan daga Alhaji Isma’il Jiƙamshi har Alhaji Sufi Garko babu sunan da bai zama mai shura ba a cikin Kano da wajenta musamman ma shi Alhaji Sufi Garko ɗin. Ƙwarai da gaske sun girgiza har mazan a yanzu dan suma dai basu san kuma amaryar tanada alaƙa da Alhaji Sufi Garko ɗin ba sai yanzu. No wander dole gwamna yay walicci kam ashe. Ƙus-ƙus ɗin da falon ya ɗauka ne ya saka Abba yin gyaran murya, a take duk sukai tsit. Abba ya cigaba da faɗin, “Kamar yanda na faɗa muku sati mai zuwa za’ai biki amarya ta tare, sai kowa yaje kamar yanda tsarin wannan gida yeke kowa ya kawo gudunmawarsa, a kuma kasance cikin shirin biki.”
“To amma yanzu Abbansu a sati guda ɗin nan har wane shiri za’ayi? Bayan kowa yasan Hydar bai ajeba bai ba ma wani ajiya ba. Gashi ya kinkimo ƴar babban gida da su komai sunfi buƙatar ganin dozin”. Mama ce da wannan magana itama dai da alama ranta a jagule yake, dan fa jin Smart ya samo ƴar babban gida ransu fal kishi da hassadar ba ƴaƴansu bane.
Caraf Umma ta amshe da faɗin, “Kema kike ta wannan ai ga zancen gudunmawa da yaywa yaran nan. Maganar gaskiya ba’ace gudunmawa ba kuma a irin wannan ƙurarren lokacin Abban su. Yanda abubuwa sukaima mutane yawa kowa na fama da kansa da iyalinsa, shi Hydar ɗin yasan bai shirya ma auren ba ya kinkimo ƴar masu hannu da shuni shi ba sana’a ba ba komai ba. inba dai sune zasu masa komai ba dan da’alama ma sadakin sune suka biya masa ko?”.
Kallonsu kawai Abba yake yi, su kansu kuma a cikin yaran duk sai sukaji kunyar abinda iyayen nasu keyi kamar wasu ƙananun yara sun kasa ɓoye baƙin cikinsu. Abba ya maida kallonsa ga Ammah da tunda ta shigo kanta a ƙasa yake baiwar ALLAH. Ajiyar zuciya ya sauke da sake maida idonsa kansu Mama ɗin. “Yalwati da Yahanasu nasan dai kun san da Aliy da yaran nan duk nawa ne ko? Kuma ni ne na bada umarnin haɗo gudunmawa kamar yanda nake basu akan kowacce hidima anan gidan tunda ba yau na fara ba. A kaf ɗinsu kuma ba gori ba babu wanda Aliy bai taka rawar gani a hidimar aurensa ba a bashi da aikin yin dai. Maganar kuma sati guda yay kaɗan ba’a shirya ba wannan komai na ALLAH ne babu ruwanku. Sannan sadaki ga ƴaƴanku nan ku tambayesu a duka aurensu ni ne na biya musu sadaki, ko akan Aliy ne zan canja abinda nake tun farko?. Ƴar babban gida kuma data tsole muku ido ALLAH ne ya bashi kasancewarsa mai ƙyaƙyƙyawar zuciya da nagarta, fatanmu ALLAH ya taya shi riƙo dan shi bai auri ƴarsu dan kuɗinsu ko sunansu ba”.
Sosai murtanin Abban ya hana kowa sake yin motsin kirki. Sai ma a cikin yaran ne maza jikin wasu yay sanyi suka shiga bama Abban haƙuri, tare da masa alƙawarin yin zaman meeting na musamman akan bikin. Albarka ya saka musu tare da sallamar kowa. Smart ne kusan ƙarshen fita, dan haka Abba yace masa bayan sallar isha’i ya samesa. Kai kawai ya jinjina masa ya ƙarasa ficewa cikin dauriya.. Fitowar tasa ta bama wasu da ga cikin ƴan uwan nasa damar tayashi murnar da suka gagara yi a ɗazun. Murmushin kawai yake musu da amsawa cikin dauriya, da ga haka ya wuce ɗakin Ammah. Ya samu Aunty Bilkisu da ƙanwar Ammah da tazo gidan babu jimawa suna tattauna abinda su Ummar sukai yanzu a gaban Abba. Yayinda su Asma’u ke ta faman murnarsu sukam finally Yayansu yayi aure shima gorin Umma ya ƙare. Gaban Ammah yaje ya zauna, yayinda Gwaggo Sa’adah ƙamwar Ammahn ta muƙe tana masa ghuɗa da kirari kasancewar sunan mahaifinsu ne ya ci, dan duk ƴan gidan su Ammah Babangida suke kiranshi ko suce Hydar, shiyyasa ma ko’anan gidan nasu Hydar ɗin ta bisa, Abba ne kan kirashi da Aliy shima wani lokacin yakance masa Baba. Idanunsa ya rumtse da sauri dan har cikin tsakkiyar ƙwalwar kansa ghuɗar nan ke ratsashi. A take kansa ya fara juyawa ya ringa ganin kamar ɗakin na juya masa shima. Ɗayan hannunsa ya kai ya ƙara dafe kan da hannu biyu. Hawwah ce ta lura da hakan, da sauri ta ce, “Yaya Hydar lafiya kuwa?”. Yanda tai maganar cikin zaburowa ya sa Gwaggo Sa’adah dakatawa, Ammah ma ta haɗiye murmushin fuskarta ta maida dubanta garesa. Aunty Bilkisu ma da ke ta faman turama dangi saƙo ta wayar Ammah ta miƙe zumbur. Ammah da ke kusa da shi ce ta samu nasarar taroshi jikinta, dan gaba ɗayansa ya tafi zai zube damma a zaune yake……
________________★
Ƙololuwar ɓacin rai Alh. Sulaiman ya shiga sakamakon kiransa da akai masa cewar ga Tajuddeen a asibiti sakamako auren Lulu da mahaifinsa ya ɗaura yau da shegen tsageran yaron nan da yakema kallon abin alhaki. Abu mafi ɗaure masa kai shine ta yaya Baban yasan da shirinsa har yaje ya ɓata masa shiri haka? Ya san dai da ga shi sai Tajuddeen suka ƙulla hakan. Dan ko mahaifiyar Tajuddeen ɗin bata san komai ba akai. To kodai cikin waɗanda ya aika sumasa waliccin auren ne? Kai bayajin hakan zata kasance ai. Dan Kawu Laminu mutum ne makwaɗaici yasan kuɗin da ya shaƙa masa bazai barsa buɗe baki ya faɗama wani ba. To ko Tajuddeen ɗinne yay ɓaranɓarama a gaban wani? Shima dai hakan bai kama hankali ba gaskiya dan yasan yanda Tajuddeen ke son auren nan bazai taɓa bari wani ya samu ƙofar rusa masa shi ba. Tattare komai yay ya ajiye gefe yabar maɓoyar tasa zuwa asibiti. Dan yazo nan ɗin ne ya ɓoye saboda Baba har sai ƙura ta lafa zuwa gobe kamar yanda ya tsara idan an ɗaura aure da Tajuddeen. Lokacin da ya isa ya samu Tajuddeen ko farfaɗowa baiyi ba ma. Ga shi labari yazo masa su baba na government house ana liyafar cin abinci bayan a gabansu Jikansa ya faɗi amma ya shure saboda bai ƙaunarsa shi da ɗansa. Sosai zuciyarsa ke ƙara tafasa, yayinda yake saƙa abubuwan alkaba’i da zai rusa rayuwar Smart da duk wanda ke tare da shi. Dan a ganinsa duk shine ya ruguza masa shirinsa, sai yanzu ma yake nadamar bayyana masa fuskarsa a waccan ranar… Farfaɗowar Tajuddeen babu jimawa mahaifiyarsa ta iso, sai dai daga zuri’arsu kaf babu wanda ya leƙo asibitin dan Baba ya hana. Ya kuma tabbatar musu duk wanda yaje sai ya ɓata masa rai fiye da yanda yake zato ko tsammani……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣5️⃣
…….Shigowar Abba da Asma’u ta fita ta kira da sauran ƴan uwansa maza da basu kai ga fitaba yasa matan darewa. Tallafosa Abba yay da ga jikin Ammah da ke tofa masa addu’a a nutsenta, duk da a rikice take amma a zahirinta babu alamar ruɗewa dan mace ce kamila mai tarin nutsuwa akan komai. Faisal ne yay hikimar matso da fanka kusa da su yana faɗin, “Ku ɗan matsa a kansa yasha iska mugani”. Fita duk matan sukai a ɗakin, sai Ammah da su Umma da suka shigo. Aunty Amarya ta ce, “Ko dai a masa hayaƙin maganin nan dan yanayin nasa kamar na matsalar can ne da ke bugunsa”. Cikin gamsuwa Gwaggo Sa’adah ta ce, “A kawo ɗin sai a gwada a gani. Rushin wuta Hawwah ta ɗibo, Maryam ta ɗakko maganin a ɗakin Ammah aka saka masa, yayinda Ammah da Abba ke cigaba da tofa masa addu’a su da sauran ƴan mazan gidan. Kusan minti talatin ana abu ɗaya kafin ya fara motsawa. Sai kuma ya fara wata irin atishawa mai ƙarfin gaske. Yayi tafi sau bakwai sai kuma ya dafe kansa yana mai ambaton sunan ALLAH da faɗin, “Ammah kimin addu’a kaina kamar zai fashe. Wayyo Ammah kaina kimin addu’a”.
Da ƙyar Ammah ta danne hawayen da suka cika mata idanu, ta kamo hanunsa cikin hannunta ɗayan kuma ta ɗaura a saman goshinsa da faɗin, “Kayi haƙuri Hydar gani nan kusa da kai ina maka addu’an in sha ALLAHU zai bari, kai dai cigaba da ambaton ALLAH”. Addu’a ya cigaba da yi a ransa, tare da sake kai hannunsa saman goshinsa ya ɗaura kan na Ammah data dafe masa… Cikin amincin ALLAH a haka aka samu barci mai nauyi ya ɗaukesa kusan gab da magrib. Abba ne ya saka ƴan mazan ɗaukarsa aka maida ɗakinsa dan zai fi samun ƙarancin hayaniya a can ɗin kasancewar nan akwai yara (jikokin gidan). Aunty Bilkisu da Hawwah ne sukaje can suka zauna da shi. Itama Ammah bayan ta idar da salla sai ta nufi ɗakin nasa da ruwan addu’oi da tayi a kofi ita da Gwaggo Sa’adah dan su Aunty balikin su samu suzo suyi salla suma……
★………..
A gaban su Baba Mawaddat (Lulu) zaune bayan ta gaishe da Baba da tunda ta shigo yake Binta da kallo fuskarsa ƙawace da murmushi. Kusa da shi da ya nuna mata ta zauna takai zaune gab da ƙafafunsa. Kanta ya dafa yana mai saka mata albarka da addu’oin zaman lafiya da mijinta da zuri’a masu albarka. Saurarensa kawai take amma ba komai take fahimta ba a halin yanzu. Sai da Baba ya gama Addu’oinsa su Uncle Yousuf na amsawa da Amin sannan ya kirayi sunanta cike da kulawa. Amsa masa tai batare data ɗago ba. Bai damu ba ya cigaba da faɗin, “Mawaddat ƴar Mawaddat yau kema kin zama babba mai kima da darajar da aure kawai ke Bama kowacce ɗiya mace a duniya. Dan daga yau zuwa ko yaushe kema za’a iya kiranki da suna UWA. Alhamdullah kin kawo mana mijin aure a jiya kuma a jiyan babu sanya muka saka akai mana bincike a kansa muka kuma ɗaura muku aure a yau kasancewar rayuwarsa cike take da abubuwan birgewa daban sha’awa irin wanda duk wasu Iyaye na gari zasuji alfaharin kasancewarsa ɗan su ko suriki. Na tayaki murna matuƙa da mu kammu ma ahalinki. Ina fatan zaki zama mace tagari da shima tashi zuri’ar zatai alfahari da ke da tarbiyyar da muka baki. Ina sake tayaki murna da tsintar dami a kala. Dan irin waɗan nan nagartattun yaran kamar Aliyu tamkar tsintar dami ne a kalla musamman idan mukai la’akari da lalacewar zamanin yanzu da matasanmu suka saka baɗala ta shaye-shaye da neman mata a gaba fiye da cigaban rayuwarsu. Fatanmu ki kasance mai biyya da haƙuri, Mun kuma ɗaura aurenki ne a wannan gaɓar babu shiri sakamakon son kwantar da ƙurar da ke son tashi, fatanmu bazakiga laifinmu ba. Sannan munyi alƙawarin shirya miki biki kamar na sauran ƴan baya da akayi hakama iyayenki gasu nan a shirye suke da shirya biki domin farin cikinki next week a kaiki ɗakin mijinki kamar kowace ƴar gatan dangi. ALLAH yay muku albarka ya jiƙan mahaifiyarki da namu iyayen muma baki ɗaya”.
Uncle Yousuf ne ya amsa da Amin shi da Uncle Khamil da Uncle Amin da suka rako Baba, sai Daddy da shima yake a falon. Uncle Khamil da Uncle Amin ma sun mata tasu nasihar. Ita dai batace komai ba saurarensu kawai take. Sai dai a ƙasan zuciyarta ayyanawa ta ke, (Grandpa kenan, kuma bar wahal da kanku ko ɓarnata kuɗinku auren wata ɗaya ne kacal. Biki kuma ko kiɗan ƙwarya babu mai mana a gidan nan). Babu wanda ya lura da halin da take ciki sai Uncle Yousuf da ke hankalce da yanda take ta faman taɓe baki duk da kanta a ƙasa yake. Dariya da tausayi ta bashi, amma sai ya kanne bai nuna ko ɗaya ba a ciki har akai zaman mata nasihar da ya san ba wai shigarta take ba suka miƙe. Rakkiya tama Baba har mota, hakan ya sake bashi tabbacin lallai tana matuƙar son wannan yaro. Sai hakan ya ƙara masa kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya dan abinda yafi fata kenan. Shi babu ruwansa da wai ɗansa ko jika sai sunyi auren ƙwarya tabi ƙwarya ɗin nan. Duk wanda kika kawo ko ka kawo iyakarsa dai yasa ai bincike. Inhar yaro ko yarinya sun fito da ga gidan tarbiyya kuma suma masu itane babu abinda ya shallesa zai bada goyon baya ya kuma sanya albarka a ciki. Hakan kuma na sake ɗaga darajarsa da kimarsa ga al’ummarsa.
Bayan wucewarsu Lulu tai komawarta ciki babu alamun wata damuwar auren tattare da ita. Daddy dai mamakin hakan yake, yayinda shi Uncle Yousuf ya san bata ɗauki abin da muhimmanci bane saboda yace mata auren contract ne. Sannan fa dama Lulu a wasu lokutan shahararriyar ƴar I don’t care ce ta bugawa a jarida duk da masifar nan tata…….
“Ita ko damuwa ma batai ba”.
Cewar Daddy cikin nuna mamaki yana kallon Uncle Yousuf. Ƙaramar dariya Uncle Yousuf ɗin yay da ɗage kafaɗu duka. Yace, “Nima abinda keban mamaki kenan”.
“Amma auta baka tsoron ko wani abu take ƙullawa. Kasan fa wacece Mawaddat akan rashin ji”.
Dariya Uncle Yousuf yayi da faɗin, “Kwantar da hankalinka babu abinda take shiryawa face sanin cewar auren na wucin gadi ne”.
“Da wannan kuma”.
Cewar Daddy cikin samun ƴar nutsuwa. Daga haka suka shige ciki dan ganawa da Mommy da yaran gidan suma duk da sudai duk sun san mike faruwa dan tun a jiya da dare Daddyn ya sanarma Mommy, Uncle Yousuf kuma ya sanarma ƴan biyu shiyyasa tunda safe suka iso Kano. Haka ma su Mubeen duk Mommy ta sanar musu a yau da safe. Sun sha matuƙar mamaki yanda auren yazo damma dai basu san dawa za’a ɗaura ɗin ba har ita Mommy ɗin sai da sukaje wajen ɗaurin auren ne suka sani, bayan sun dawo ɗinne sukai zaman jinjina al’amarin.
Kallan kallo aka shigayi tsakanin Mommy da ƙannen Lulu jin wai da Smart drivern ta akai ɗaura mata aure yau. Karan farko Hussain yay murmushi har haƙoransa na bayyana bayan Mubeen ya gama basu labarin yanda take yaga Smart ɗin. Duk da ganin harar da Daddy ke masa bai iya haɗiye abinda ke bakinsa ba sai da yace, “Uncle You kuma itace tace tana son sa da kanta?”.
Murmushi Uncle Yousuf ɗin yayi shima da faɗin, “Hussain ai matar mutum kabarinsa inji hausawa. Fatan alheri yanzu suke buƙata garemu baki ɗaya. Sannan kuma sai kuyi himmar naku auren dan zamanku haka ya ishemu. Dan haka na baku da ga nan zuwa ƙarshen shekara inba haka ba kuma mu koma Jiƙamshi a duba a cikin dangi ni babu ruwana”.
Dariya Mubeen ya shiga tuntsurawa, su Amrah na tayashi ƙasa-ƙasa dan suna tsoron ta fita aci ƙaniyarsu. Da ga haka kuma aka cigaba da hira, ganin hirar na daɗi babu Lulu kuma Uncle Smart ya aika Suhaib yay kiranta. Koda ta fito taga har da su twins sai tai kamar zata koma. Sai dai kiran da Uncle Yousuf yay mata ya sata dole ƙarasawa. Kamo hanunta Mommy tai ta zaunar a kusa da ita tana murmushi. Ta ce, “Haba yarinyata miyasa zaki koma kuma?”.
Kasancewarta ba mutum mai ɓoye-ɓoye ba ta ce, “Mommy to bakowan kesan ganina anan ɗin ba. Kinga babu amfanin na zauna ko”.
Karan farko Mommy taji wani iri a ranta, dan yanda Lulu tai maganar cikin rashin sakewa zai tabbatar maka halin ko’in kula da ƴan uwan nata ke nuna mata yana cimata rai matuƙa musamman su manyan. Shi kansa Uncle Yousuf wani tunani ne ya fara zo masa a rai akan furucin nata. Daddy kuwa tuni fuskarsa ta nuna ɓacin rai, ya bi su Hassan ɗin da wani irin mugun kallo. Sai kuma ya miƙe tare da zuwa har gaban Mommy ya kama Hannun Lulu ga miƙar. “Tunda basu son ganinki sai suzo su kasheki ai Mawaddat, sannan su haɗa da ni nima” ya jata suka fice a falon. Babu wanda ya iya cewa komai sai Uncle Yousuf ne da ya kafe su Twins ɗin da kallo ya furzar da iska. “You see wannan shine abinda nake ta so ku fahimta tun ba yanzu ba. Amma sai kuka kasa fahimtar tawa saboda idonku ya rufe da cewar Yaya baya son ku sai Mawaddat. Anji shi kan kuskure yake, amma koyaya dai mahaifi sunansa. Amma ita minene laifinta tunda ba itace tace yay mata hakan ba tun bata san kanta ba. Sannan har yanzu Mawaddat bata san minene ya faru kafin haihuwarta ba, ta yaya zaku dinga hukuntata da laifin daba ita tayi ba. Duk da rashin jinta da ake gani a ranta tana matuƙar son kusanci da ku, sai dai rashin damar da kuke bata yasa ta zaɓi kaɗaice kanta bata da wani amini sai Yaya a gidan nan”.
“Amma Uncle ai Mommy ta jata a jiki Daddy yay katanga ma hakan saboda yana ganin zata cutar masa da ƴar gwal”. Hassan ya faɗa cikin ɓacin rai dan yanada zafi. Murmushi mai ciwo Uncle Yousuf yayi, “Yes Aunty Khareema ta jata Yaya yay ƙoƙarin hana hakan, amma ai ba Mawaddat bace ta ƙi aunty Khareema ko. Ku zauna kuyi nazari akan wannan matsalar kuma Kanada taku gudunmawar a ciki, sannan a yanzu na ƙara fahimtar a fanɗarewar Mawaddat harda dalilin ɗaukar kanta ware da kuke nuna mata. Ku manyanta ne, kun fita hankali da sanin ya kamata, ku kuma ajiye halin Yaya gefe ku zauna kuyi nazari akan duk abinda ke faruwa a tsakaninku da ita kuyi alƙalanci tun kafin kuzo kuyi nadama da ga baya”. Da ga haka ya miƙe batare da jiran cewar kowa ba yay ficewarsa. Shiru falon kowa ya kasa cewa komai, dan hatta Mommy kalaman Uncle Yousuf ɗin sun shigeta. Sai take gani kamar itama tana da nata kamshon mai girma da bata taɓa zama wajen matsa musu canja abinda suke kallo ba yanda yake faruwa ba tunda Mawaddat dai ba ita yace Daddy yay mata irin wannan rikon ba, sannan yarinyar bata taɓa ƙin ƴan uwan nata ba, barta dai da tsiwarta sai kuma gatan da Daddyn ke nuna mata na fitar hankali sama da sauran yaran a komai na rayuwa………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣6️⃣
…….Gaba ɗaya hankalinta a tashe yake, duk yanda take ta son dannewa hakan na neman gagara. Ga shi Kasancewar ƴaƴanta na nan ta rasa ta yanda zatai kiran aminiyar ta su tattauna wannan ruɗani da ke neman kaita ƙasa a yinin yau. Ganin hankalin duk jama’ar gidan ya koma kan halin da Smart ke a ciki ya sata sirarewa ta koma ɗaki. Can ƙuryar ɗakinta ta shige ta rufo. Takaicin yanda wayar keta ringing anƙi a ɗauka ya sata jin kamar ta kaima bango naushi. Sake kira na biyu tai bayan katsewar na farkon. Yanzu ma har ta fidda rai da za’a ɗaga ɗin, amma jin an ɗauka ya sata sakin wata wawuyar ajiyar zuciya. Cikin haushi da ƙosawa ta ce, “Haba Hajiya Naqiba ina kika shigane ke kuwa inata kiran waya..”
“Yi haƙuri ina falo ne da mutuniyarki, wai munafukan tazo tana faɗa min tsolon ƴar nan tata ragowar ciwo ta samu miji amma Alhaji ya ƙi saurarenta, acewarsa sai ta gama makaranta fa maganarsa ba canji”.
“Mtsoww aikin banza. Banda haukarta ma wannan sikila ɗin ko auren tai dawo mata zatai”.
“Hhhhh ashe kin gane Aminiya. Shiyyasa mafa ni yarinyar sam bata cikin lissafina wlhy……..”
“Aminiya ina cikin tashin hankali wlhy yau ɗin nan, tun ɗazun na rasa taya zan kiraki ɗaki cike da Ƴaƴa kin san yau juma’ar ƙarshen wata”. Umma ta katse ƙawar tata Hajiya Naqiba.
“Tofa mike faruwa kuma Aminiya. Ke da kin gama kame gida tsaf baki da wata matsala a yanzu, banda ma waccan shegiyar sirikar taki matar Salim na neman buɗe mana aiki itama….”
“Aminiya masu son buɗe mana aikin ai sun ƙaru. Kin san shegen yaron da muka cimmawa da ƙyar yau Alhaji ya ɗaura masa aure……”
“Aure kuma? Wai kina nufin ɗan wajen Hafsatu”.
“Aminiya inba shi ba wane shegen tantirin yaro ne ke bani wahala a gidan nan. Kedai shaidace akan kuɗin dana dinga kashewa ga al’amarinsa sai da ƙyar muka samu malamin nan na zuru yay mana aikin da ya ci. Yau kuma wai sai ga Alhaji da wannan mummunar labari, abu mafi ƙona rai ka ƴar masu garin Kanon fa……” ta kwashe komai ta sanar mata har halin da Smart yake a ciki yanzu.
Sosai Hajiya Naqiba ta jinjina al’amarin. Dan tasan aikin Malam na-zuru kam garanti ne. Cikin jimami da taya ƙawar tata takaici ta ce, “A lallai dole ki shiga ruɗani Hajiya Yahanasu. Kuma bamuga ta zama ba dole mu shiga Zuru a gobe. Ƴar gidan Alhaji Isma’il Jiƙamshi fa? Kin san kuwa wanene wannan mutum? Shahararren mai arziƙi ne wlhy balle kuma wai jikan Alhaji Sufi Garko masu juya ƙasar nan a yanda suke so. To banda masifa ma irin ta wannan hatsabibin yaron ina ma suka haɗu? Ai in har kuka bari wannan yarinyar ta tare to kun gama kaɗewa, dan Hafsatu ta gama yi muku fintinkau. Shi ko kinga ai batun wani ƙwallo ya ajiye kuma ga komai a gashe sai dai ci. Ai ko ƙasar nan bana zaton zai cigaba da zama kuma….”
“Aminiya kina ƙara rikitani wlhy. Bakiji yanda kaina ya ƙara ɗaukar zafi ba. Yanda na tsani mutuwata haka na tsani yaron nan a gidan nan dan na jima da fahimtar son da Alhaji ke masa. Ga abinda malamin can ya faɗamin a kansa tun yana ɗan ƙaraminsa…….”
“Kinga ki kwantar da hankalinki, kawai dai duk ma yanda za’ai kiyi gobe ki fito muje mu wajen Malam Na-zurun”.
“To shike nan. Bari naje kar a juya ba’a ganni ba kuma a zargi wani abun kin san dai munafukan matan gidan nan musamman ma shegiyar Fatin can (aunty amarya) da take abu kamar Hafsatun ce ta haifeta, na rasa mitai mata masheranciyar take mata irin wannan biyayyar itama shegiyar ta biyu”.
“Duk zamuyi maganinsu. Itama sai a kaita ai gobe a sabunta mana aiki a kanta kawai.”
Sosai Umma taji daɗin wannan shawaran. Dan haka ta ƙara jerama aminiyar tata godiya sannan sukai sallama jin Hannatu ƴarta na ƙwala mata kira da ga falo…..
(Ke kuma Umma haka kike ashe. ALLAH ya rabamu da ɓatan basirar zamowa mushrikai akan kishi da abin duniya🤦, duk abinda ka gani rubutacce ne da ga ƙaddarar mutum. Kai baka isa canjashi ko sakawa ba. Dan mi zakaita wahal da kanka da ɗorama kai zunubi ga asarar kuɗi. ALLAH ka shiryar damu dai🙏).
____________________
A falon Daddy Uncle Yousuf ya samu Mawaddat kwance, yanda tai lamo sai ya fahimci kamar kuka ma tayi. Tausayi ta bashi, dan zuwa yanzu ya ƙara fahimtar akwai wani tabo a zuciyarta da take ɓoyewa kuma ya kamata ace sun sani. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da aro murmushi ya azama fuskarsa yana kaiwa zaune da kiran sunanta. Idanunta da ke a lumshe ta buɗe tana kallonsa. Sai kuma ta tashi zaune fuskarta har yanzu da alamar damuwa ta ce, “Uncle You sai yaushe ƴan uwana zasu daina jin tsananta ne?. Na rasa mina musu da girma haka. Na rayu ba’a cikinsu ba, kullum cikin begen son ganinsu neke a zuciyata duk da basu taɓa zuwa inda nake ba sai a hoto idan ka nuna min su. Amma sanda na iso da zumuɗin ganinsu fuskar da suka fara tarbata da shi shine na tsana. Har yanzu kuma irin wannan tsanar nake gani a cikin idanunsu bata taɓa sauyawa ba. Su Amrah ne kawai ke sakewa da ni, suma a wasu lokutan nasha samunsu suna zagina sai dai ban taɓa nuna musu na sani ba. Kodai dan ba Mommy ta haifeni ba kamar su shiyyasa basa sona….”
Kai Uncle Yousuf ya dafe, sai kuma ya ɗago duk a lokaci guda yana girgiza mata kansa. “No Mawaddat ba haka bane ba. Amma ina so ki kwantar da hankalinki zamuyi magana a nutse. Ni yau ɗin ma naga duk kin zama kamar wata raguwa kamar bake ba. Bakin duk ya mutu kar fa Aliyu yay miki dariya idan ya ganki haka yay zaton kin karaya ne”.
Baki ta tura gaba tana yamutse fuska. “ALLAH ya kiyaye Uncle You. Ni kawai yau bana jin daɗin raina ne. Ni bari ma na shiryo na bika wajen Aunty Saliha nai weekend a can kawai”. Kafin yace wani abu harta fice a falon. Ya buɗe baki zai kirata Daddy da ke fitowa a ɗaki yace, “Yousuf barta kuje can ɗin kawai.”
“Yaya yanzu fa tana da aure. Kasan ko bai dace ba. Amma ina zuwa ”. Yay maganar yana zaro wayarsa. Idanu Daddy ya tsira masa cike da zargi, sai dai bai ce komai ba. Tsaf Uncle Yousuf ya lura da shi, amma yay biris ya cigaba da kiran no ɗin Smart. Sai dai har ta yanke ba’a ɗaya ba. bai gajiya ba ya sake kira. Maryam ce ta ɗaga, cikin nutsuwarta tai sallama tare da gaishesa. Sannan ta ɗora da faɗin, “Yayan baida lafiya ne”.
Cike da mamaki Uncle Yousuf yace, “Baida lafiya kuma? Aliyu fa nake nema”.
“Eh shi ɗin”. Ta sake faɗa da ladabi. A rikice Uncle Yousuf ya ce, “Ya salam miya samesa? Yanzu fa babu jimawa muka rabu da shi. Kinga ina zuwa”. Ya faɗa yana yanke wayar. Number Abba yay kira, bugu biyu kuwa ya ɗaga suka gaisa da sakema juna bangajiya. Sannan Uncle Yousuf ya ɗaura da tambayar abinda ke bakinsa. A nutse Abba yay masa bayanin komai, tare da ɗorawa da faɗin, “Al’amarin Aliy ya fara bani tsoro a wannan gaɓar, dan in har ba shafar junnu ba to lallai dole akwai sihiri mai ƙarfi jikin yaron nan. Dan sai a yau na sake fahimtar wani abu. Halan ma auren da muketa matsa masa yayi amma yaƙi duk akwai dalili, sai yau da ALLAH ya kawo iyaka akayin kuma yazo cikin bazata shine hakan ta kasance?”.
Numfashi Uncle Yousuf yaja mai ƙarfi. “Tun lokacin da Hameed ya bani labarinsa na fahimci makamancin hakan gaskiya. Kuma malamin nan dama ya faɗa cewar sihirine mai ƙarfi tattare da shi wanda aka ƙulle duk al’amarin rayuwarsa masu girma. Sai dai kuma addu’a tafi ƙarfin komai da kowa, wata rana duk ƙarfinsa zai zama ya warware in har aka cigaba da gayama ALLAH shi maji roƙon bayinsa ne. Kuma insha ALLAHU muna fatan warwarewar lamuranne suka fara zuwa”.
“To ALLAH ya tabbatar da hakan Yusufa”.
“Amin ya rabbi malam. In sha ALLAHU yanzu zan zo gidan tare da malam ɗin ku kwantar da hankalinku”.
Bayan Uncle Yousuf ya ajiye wayar yayma Daddy bayani. Shima ya nuna alhini da jin tausayin Aliyun. Sai kuma ya ɗora da faɗin, “Maganganinka sun sani a ruɗani fa akan yaron. Har kayi masa sani irin haka dama Yousufa?”.
“Yaya na san fiye ma da haka akan Aliyu. Sai dai yanzu bamu da lokaci, amma ka bini bashi wataran zan maka bayani insha ALLAHU”.
Daddy bai ja zancen ba kawai ya gyaɗa masa kai da ƙara yima Smart addu’ar samun lafiya. A haka Mawaddat ta dawo ta samesu. Bai mace mata komai ba sukai ma Daddyn sallama suka wuce. Ko a hanya bai sanar mata halin da Smart ɗin ke ciki ba ya kaita gida ya ajiye. Sai dai bai shiga ba ya koma shi ita kuma ta shige cikin cike da zumuɗin son ganin Deen ɗin ta. Dan tana matuƙar ƙaunar yaron ita dai…
Bayan sallar magrib kaɗan Uncle Yousuf da Hameed (Coach) suka iso gidan tare da Malam da sukaje har gida suka ɗakko. Har ɗakin Smart ɗin suka shiga bayan su Gwaggo Sa’adah sun fito. Malam ya ƙara masa addu’a sosai tare da kwantar musu da hankalin in sha ALLAHU komai zai dai-daita. Yau ɗin ma dai ruwan addu’oin nan ya sake basu da sake jaddada musu dage masa da addu’a shi kuma ya ƙara dagewa da yin azkar da sadaka. Har suka bar gidan Smart bai farka ba yanata barci, sai kusan ɗaya ya farka da azababben ciwon kan da dole sai da aka nemo wani ma’aikacin asibiti a anguwar saboda yanda yake ta complain kansa kansa kamar zai fashe. Dubasa yay da yi masa allura ya kuma saka masa ƙarin ruwa sannan aka samu wani barcin mai nauyi ya sake yin gaba da shi………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣7️⃣
…….*_WASHE GARI_* da asuba da ƙyar Lulu ta iya tashi sallar da Uncle Yousuf ya sa aunty Saliha ta tadata yi. Dan kuwa dai daren jiya suna gama hira da Aunty Saliha ta shige ɗaki sakamakon dawowar Uncle Yousuf gidan a gajiye ta samu sirof ɗin ta da wani ya kawo mata a gidan bayan sallar isha’i ta fita a sulale ta amso bada sanin aunty Saliha ba har kwalba uku tasha. Dan yanda kanta yau ya ɗauki zafin nan ta tabbatar sai tazo kwanciya komai zaita dawo mata a rai ta kwana cikin damuwa. Sam bata buƙatar hakan kuma. Ga shi dama abin yazo mata a dai-dai wato weekend. Dan dama fa duk weekend kusan sune ranakun da tafi ƙwalewa son ranta ta sha barcinta. Kafin a gane tana shaye-shaye sai aita ɗauka gajiyar aiki ce ke sata mahaukacin barcin da take sha. Balle ma Daddy kan hana a tadota a cewarsa a barta ta huta. Hakan na bata dama ƙwarai da gaske ita kuma ta sha abinda take son batare da sun gane komai ba.
Sabon barci ta sake dasawa har kusan sha ɗaya sai da Uncle Yousuf nan ma yasa Aunty Saliha tadata. Tun a yanda ta fito ya fahimci wani abu ta sha a jiyan, bai ce komai ba kan haka duk da zuciyarsa tayi babu daɗi sai cemata da yay ta koma ta shirya yana jiranta zata rakashi wani waje. Kai kawai ta gyaɗa masa da komawa ɗakinta dan tana da ɗaki dama a gidan. Ta jima a toilet ɗin kafin ta fito tanata ƙamshin shower gal mai ƙamshin tsiya, dan anan bata da turarrukan wanka duk ta ƙarar da su ta kuma manta ta kawo ta ajiye dan bata iya cikakken sati biyu batazo nan ta kwana ba ko yin weekend. Tana tsaka da shiryawa Deen ya shigo. “Akku mai bakin magana kenan”. Ta faɗa tana kallonsa. Ai ko yay zaman dirshan ya fara tsiyaya mata surutu itako tana biye masa dan kaf ƙannen nata tafi ƙaunar yaron fiye da kowa. Shima kuma yana son aunty Lu ɗinsa. Sai da ta gama shirinta tsaf cikin doguwar riga ta atamfa da tai masifar lafe mata a jiki kamar wadda akaima fenti. Dan Lulu koda ta saka kayan hausawa irinsu lass atamfa material zaka samesu dai babu wani ɗinkin mutunci a tare da su. Shiyyasa ma kayan basa wuce fitet gwan ne. Dan ko skert da riga ba sosai ta cika yi ba, inma tayin zaka samu suma dai sai sun mata ɗamm kamar zatai nishi su yage. Kasancewar kuma tana da ƙyaƙykyawar sura sai sukan mata ƙyau kamar an haliccesu a jikin nata ne. Dan telan nata kam ƙwarone wajen iya ɗinkin shegantaka. Ba kuma kowa ya haɗata da shi ba sai Nadiya. Yau ma ko takan ɗan kwali ba’abi ba dan dama Amrah ce a mafi yawan lokaci kan mata ɗauri idan tai irin wannan dress ɗin. Sirrin mayafi milk color da ya shiga da zanen atamfar ta yana kawai bisa kai aka ɗora ƙaton google tare da dogayen takalmanta. Dan ƙyau kam tayi ƙyau ga wani mahaukacin ƙamshi mai ɗaukar hankali na tashi. Uncle Yousuf bai fito ba harta kammala breakfast da ba wani na kirki taci ba. Dan shaye-shaye ya gama cinye Lulu ko abincin kirki bata iya ci a rayuwarta. Barta da son cin chocolate kamar shazumamu, dan ko a handbags nata baka rabata da su bayan ƙwayoyinta na shaye-shaye. A tare aunty Saliha da Uncle Yousuf suka sakko da ga sama. Dan haka su duka suka zuba mata ido. Aunty Saliha ce ta fara faɗin, “Babyn Uncle badai da kayan nan zaki fita ba musamman ma ɗan mayafin nan?”.
Sosai mamakin furucin aunty Saliha ya sata waro idanunta manya da suka juye. Sai kuma ta kalla kanta. Dan tasan dai ba yau ta saba fita a kahaba ai. “Mamy miye laifin kayan nan kuma?”. Ta faɗa fuska a turɓune. Murmushin aunty Saliha tayi da faɗin, “Haba dai Mawaddat ai yau ba jiya bace. Ko kin manta yanzu ke matar aure ce”.
Wani mugun yamutse fuska tayi dan ita tama manta da wani batun auren. Musamman da ya kasance abinda tasha a daren jiyan ya mantar da ita duk wata damuwarta. Kamar Zatai magana sai kuma tai shiru jin Uncle Yousuf yay gyaran murya da faɗin, “Kinga barta kawai muje ai a mota ne, kuma babu inda zata fita sai a can”.
Sosai aunty Saliha ta zubama mijin nata ido da mamakin abinda ya faɗa. Dan abu ne da batai zaton ji daga garesan ba sam. Kasa sake magana tai har suka fice Lulu na mata bye ita da Deen da ya maƙale zai bita. Ta ja ajiyar zuciya da faɗin, “Ai masa sannu sai kun dawo”. Da kai kawai Uncle Yousuf ya amsa mata yana ficewa. Yasan abinda yay ɗinne ya ɗaure kanta. Sai dai shima yanada hikimarsa tayin hakan bawai bai san abinda yake yi bane.
A motar tuƙinsa yake tayi, yayinda ita da Deen suketa surutunsu da dariya. Dan indai Lulu da Deen ne kam babu mai shiga tsakani. Sai ya ƙulleta da haushi ta mammakesa da kiransa mai shegen surutu kamar akku. Sun tsaya a wani ƙaramin super market Uncle Yousuf ɗin ya fita shi ɗaya. Bai jima ba ya dawo, sai kuma a wajen masu fruits, nan kam da ga motar ma yay bayanin abinda yake so aka kawo masa ya bada kuɗin suka cigaba da tafiya. Lulu dai bata tambayi ina zasuje ba. Hasalima hankalinta gaba ɗaya naga Deen ne. Sai da motar ta tsaya ne sannan hankalinta ya dawo ga inda suken. Kallon anguwar take a ɗan yamutse, duk da ba wani datti bane ko makamancin hakan, hasalima titi ne shimfiɗe da ya miƙe samɓal kasancewar gidan su Smart na a farkon shiga layinne. Sai dai yanayin gine-ginen da kai kawon mutane dana ababen hawa riiiii yasa zaka tabbatar dai irin tamu ce dangin malam Shehu….
“Papa nan fa?”
Cewar Lulu a gatsine.
Maimakon bata amsa wayar da yake dannawa ya kai kan kunne. Ta daiji yana amsa gaisuwa, sai dai bata fahimci mi ake cewa da ga can ba. Sai kuma taji Uncle Yousuf ɗin na cewa, “Kai dai kaɗai ne a ɗakin ko? Okay gani nan shigowa”. Daga haka ya yanke wayar tare da buɗe murfin yace, “Oya ku muje”.
“Uncle…..”
“Shiiiii…” yay saurin katseta tare da mata alamar zip a baki. Dole ta haɗiye abinda take son fadar dan babu alamar wasa akan fuskarsa. Shi da kansa ya kwashi ledojin, ita kuma ta fito riƙe da hannun Deen tana ta faman yamutse fuska. Sauƙin ma babu kowa a ƙofar gidan. Wanda ke iya hango su kuma ba sosai suke iya ganinsu ba duk da harda masu leƙe saboda son gulma irin ta mutane. Soron ta dinga bi da kallo duk da shima dai fes yake gashi kuma lailaye da sumintinsa. Hakama koda suka shigo gidan ko’ina fes babu wani datti, ga gidan shiru babu yawan hayaniya sosai dan yaran sun wuce ismaliyya, sai ma matan anguwa da wasu a dangi dake ta faman shigowa yin ALLAH ya sanya alkairi da auren Smart ɗin da ba’a san da shi ba. Sai kuma wanda suka san baida lafiya na ɗorawa da jajanta yaya jiki musamman maƙwafta. Anan dai ta inda suke basu haɗu da kowa ba har suka shige sashen ɗakunan samarin gidan da ke a farkon shiga. Anan sun ɗan haɗu da wasu. Bakowa bane kuma sai Mubarak da kema Smart wankin kayansa na ciki, sai Abdull a gefensa yana kallon film a waya da eirpiese a kunnensa. Mubarak ya shiga musu sannu da zuwa cikin girmamawa dan ya gane Uncle Yousuf, itako Lulu dama kallo guda tai musu ta ɗauke kai gefe a ranta tana ƙunƙunin ina ne nan Uncle You ya kawosu. Duk da dai gidan babu wani makusa tare da shi a ɓangaren tsafta a ginensa dai na masu ƙaramin ƙarfi ne. Ita ba hakanne ya dameta ba, kawai bata cika son zuwa irin wajejen nan bane, shiyyasa ko aikinta ya ratsa da hakan zaka ganta cikin rashin sakewa da son a gaggauta abar wajen. Abdull da Mubarak ya zungura shima ya shiga gaishesun. Duka dai Uncle Yousuf ne ya amsa da tambayarsu ko Aliyu na nan? Duk da yasan yana nan tunda dai yayi waya da shi. Sun amsa masa da girmamawa Abdull ya tashi yay musu iso.
Tunda Uncle Yousuf ya ambaci Aliyu ta kafesa da idanun son jin ƙarin bayani, sai dai bai kulata ba yay gaba dole suka bisa a baya. Yana zaune a saman katifarsa da ƙarin ruwan da doctor ya ƙara saka masa babu jimawa saboda rashin ƙarfin jiki da ya tashi da shi. Wando ne 3 quarter a jikinsa da ƙaramar t-shirt data kama masa jiki sosai. Ainahinsa na tsayayyen mutum ya fito sosai. Fes ɗakin yake ga ƙamshin turaren wuta mai daɗi da Maryam ta saka masa bayan ta share. Gefensa kaɗan flaks ɗin shayinsa ne da cup da ya sha sai kayan tea a wani basket mai ƙyau harda bread alamar dai nan ɗin ne wajen ajiyarsu. Sai kuloli biyu da jug mai riƙe zafi da aka dama masa kunun gyaɗa. Sallamar Abdull da ta Uncle Yousuf ta sashi ɗago idanunsa da ke kallon tv ya zubama ƙofar tare da amsawa. Abdull ya fara shigowa da faɗin, “Yaya Smart baƙi ne”. Kalmar baƙin ta bashi ɗan mamaki, dan shi a tunaninsa Uncle Yousuf ɗin ne kaɗai kasancewar su Daddy basu jima da tafiya ba su. Kafin ya kai ƙarshen tunaninsa Abdull ya gama ajiye ledojin da ya amsa a hannun Uncle Yousuf Deen ya shigo, Uncle Yousuf biye da bayansa Lulu a ƙarshe. Harga ALLAH sai da gabansa ya faɗi, bawai na tsoro ko makamancin hakan ba, shi dai kawai ya samu kansa da jin bugawar ƙirji. Sai dai kuma abinda bai sani ba bashi kaɗai ba. Ita kanta Lulun sai da nata ƙirjin ya harba. Hannu ya miƙama Deen yana faɗin, “Welcome my little handsome”. Cike da farin ciki Deen ya nufesa shima yana murnar ganinsa. Zama Uncle Yousuf yay a sofa ɗin ɗakin ƙwara ɗaya yana murmushi, yayinda Lulu ta wani cakuɗe fuska da yamutse ta duk da taji shock ɗin ganin inda Uncle You ɗin ya kawo ta ta danne, dan tunda tai masa kallo ɗaya a yayin shigowarsu bata sake ba.
Smart da ke sauraren surutun Deen da ya karaɗe ɗakin ya dubi Uncle Yousuf cike da girmamawa ya ce, “Uncle Barka da safiya”.
Shima cike da kulawa yake kallonsa da tausayawa. Amsawa yay da “Barka dai Aliyu yaya jikin naka?”.
“Alhmdullah ai na miƙe”.
“Kana dai dauriya Aliyu ga shi harda su ƙarin ruwa. ALLAH ya baka lafiya yasa kaffara ne”.
“Amin ngd”.
Ya faɗa can ƙasan maƙoshi yana bin Lulu da ta dogare tsaye da kallo ƙasa-ƙasa. A take wani abu ya tokare masa maƙoshi akan shigar jikinta. Lallai yasan akwai babban yaƙi a tsakaninsu. Dan shifa bazai yarda da wannan shigar shegantarkar ba gaskiya. Uncle Yousuf da shima ya juya yana kallon Lulun ya nuna mata gefen katifar yana faɗin, “Zauna mana kikai mana tsaye a kai Mawaddat. Ba kuma kiga Aliyu babu lafiya ba?”.
Kamar zata fasa ihu taji, ta sake yamutse fuska da ɗaureta a taƙaice ta ce, “Uncle nan ma it’s ok”. Sai kuma ta dubi Smart fisha cike da gatsali ta ce, “Sannu fa”…….✍️
*_Kuma sannu fa🙋 dangin Smart 😂🤣🤩. Dangin mu Lulu’s team Barka da rana😚😘😉._*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣8️⃣
……..Bai nuna ma ya jita ba balle ta samu amsa. Sai ma sake tattara hankalinsa da yay ga Deen. Uncle Yousuf ne yay mata nunin ta zauna cikin harara. Zaunen ta kai a ɗofane gefen katifar kaɗan badan taso ba. Bayanin da Smart ke masa na cewar su Daddy sunzo da twins da Mubeen har da su Suhaib sun dubashi babu ma jimawa suka wuce ya sashi maida hankalinsa garesa.. har cikin rai yaji daɗin hakan, dan baiyi zaton Yayan nashi zai yi wannan abin kirkin ba. Da ga haka suka cigaba da ƴar hira jefi-jefi. Kusan mintuna goma Lulu dai na zaune tana bin ɗakin da kallo ƙasa-ƙasa, sai dai duk ta matsu su wuce amma taga Uncle Yousuf baida niyyar ma hakan. Dan hankali kwance suke hirarsu kamar ma sun manta da ita a ɗakin. Deen kuwa yay matashin kai da ƙafarsa yana buga game ɗin ball da yace ya kunna masa dama shine tushen amintakarsa da yaron tun farkon fara aikinsa. Kiran wayar Uncle Yousuf da akai ta katse musu hiran, tashi yay ya fita a ɗakin domin amsawa.
Shiru ɗakin ya ɗauka baka jin komai sai hayaniyar game ɗin da Deen ke bugawa. Dan tvn ma da ke aiki dama ƙasa-ƙasa ƙararta take. Sosai yanzun kam ya zuba mata ido duk da iya bayanta da ɗan gefen jikinta zuwa fuska kawai yake iya gani, ƙasa-ƙasa yay ƙwafa da ɗaukar ƙaramar wayarsa da ke gefe yay ɗan danne-danne ya kai kunne. Ana ɗagawa da ga can a cinkunshe ya ce, “Bama Nasreen ta kawo min hijjab”.
Da mamaki Maryam ta ce, “Yaya Hydaar hijjab kuma?”. Ƙitt ya yanke kiran batare da ya amsa mata ba. Kafin ya ajiye wayar kira ya shigo, Uncle Yousuf ne dan haka ya ɗaga. Kafin ma yace komai da ga can Uncle Yousuf ɗin ya ce, “Aliyu am sorry ina ɗan zuwa bazan jima ba uzirin gaggawa ne”.
“To Uncle ALLAH ya tsare sai ka dawo”. Da ga haka ya ajiye wayar. Dai-dai nan Nasreen tai sallama. Duk da ƙarancin shekarunta bata shigo ba sai da tace, “Uncle in shigo?”.
“Eh Angel”.
Ya bata amsa idonsa a kan ƙofar. Lulu da muryar yarinyar ta ɗauki hankalinta itama ta zubawa ƙofar ido. Sai ko gata ta shigo hanunta ɗauke da gogaggen hijjab fari da keta tashin ƙamshi. Ɗan tsayawa tai tana ma Lulu da ta zuba mata ido kallon rashin sani. Sai kuma ta ce, “Aunty ina kwana”. Batare data jira amsawarta ba ta nufi Smart, sai dai tana tafiyar tana ɗan waigowa ta kalli Lulun, dan ita dai ƙaton gilashin data toshe fuska ne mafi ɗaukar hankalinta. Karan farko Lulu ta saki murmushi tun shigiwarta ɗakin, sai kuma ta sa hannu ta cire gilashin dan sosai ƴar yarinyar ta tafi da hankalinta. Kodan basu da baby girl kamarta a gidansu ne oho. Sanda su Afrah suke kamarta kuma bata Nigeria. Zamanta ta gyara ta yanda zata fuskanci Nasreen da ƙyau, hakan kuma sai ya bata damar fuskantar Smart, dan ta fuskanci katifar ne kai tsaye shi kuma yana a gicciye ne.
“Baby Girl how are you!”.
Ta faɗa tana kai hannu ta kamo na Nasreen da ta gama miƙama Smart hijjab ɗin da ta kawo. Yarinyar sai da ta kalli Smart fuska a ɗan ƙwaɓe, ya ɗaga mata kai ciki lumshe idanu alamar taje sannan ta dawo da kallonta ga Lulu a hankali ta ce, “I am fine”.
A zuciya Lulu tace (tofa ashe tana jin turanci) a zahiri kam sai ta matso ta jikinta. Ga dai yarinya fess kuma ƙyaƙyƙyawa, amma batai zaton samunta wai tana jin yaren turanci ba. da turancin ta sake tambayarta sunanta. Nan ma ta amsa mata tsaf, ta tambayeta shekararta nawa, ajinta nawa kuma a makaranta. Nan ma ta bata amsa dai da turancin. (Ikon ALLAH) ta sake faɗa a zuciya. A karan farko kuma ta dubi Smart da ya zuba musu idanu. Da farko dai magana tai niyyar yi, sai kuma tuna dawa take a ɗakin ta fasa dan yanda ya zuba musu ido ga kayan jikinsa da haka kawai suka sakata jin wani iri, ɗauke idanunta tai da ɗaukar Nasreen cak ta maida saman cinyarta ta zaunar. Nasreen ta kallesa a ɗarare ta ce, “Uncle wacece ita auntyn nan ban santa ba?”.
“Kema wacece ai bamu sanki ba?”.
Cewar Deen cikin tare numfashin Nasreen cike da haushin hawa masa cinyar Aunty Lu da tayi. Aiko Nasreen ta balla masa harara shima ya rama yana kaina ƙafarta tsunguli. Doke masa hannu Lulu tai da faɗin, “karka taɓa min Baby”. Baya yaja yana tura baki. Smart ya riƙosa yana murmushi. “Kaga ƙyalesu kaima ba gaka da ni ba”. Dariya yaron yay da faɗin, “Yes Uncle” sai kuma yayma Nasreen gwalo. Itama ramawa tai da faɗin, “Ai dai Uncle ɗina ne, kuma yafi so na”.
“Mai ƙarya yafi sona. Ko Uncle Smart?”.
Deen ya faɗa kamar zai yi kuka. Murmushi Smart yay masa da gyaɗa kai. Cikin raɗa ya ce, “Ai namiji na namiji ne, mace kuma ta mace. Itama ga aunty ta samu. Kaga 1-1 kenan. Dan haka kuyi gaisuwa banda faɗa”. Dariyar jin daɗi Deen yayi, tare da miƙama Nasreen hannu. Sai yarinyar ta maƙe kafaɗa da faɗin, “Halamun ne gaisawa da maza, a islamiyya an faɗa mana duk mai gaisawa da maza za’a sashi wuta. Ka gaisheni dai a haka. Ko aunty?”.
Matuƙa gaya Nasreen ta burge Lulu, fuskarta da murmushi mai ƙayatarwa ta gyaɗa mata kai. “Hakane sweet heart”. Cikin jin daɗi Nasreen tace, “Kaji ko”.
“Ai nima an faɗa mana a Islamiyyar mu”. Cewar Deen shima. “Lah da gaske? Zo muje to kaga littafaina”. Nasreen ta faɗa itama. Babu musu Deen ya miƙe yana ajiyema Smart wayarsa akan jiki. Itama sai ta tashi suka fice a tare.
A hankali Lulu da ke binsu da kallo cike da sha’awa ta wani lumshe ido fuskarta da murmushi har sannan. Idanunsa masu kaifi ya zuba mata, sai kuma a hankali ya motsa lips ɗinsa wajen faɗin, “Kin fara tunanin kema nan da 5years kina da kamarsu ne?”.
Idanun ta buɗe da sauri a kansa tana haɗiye murmushin fuskarta. Sai kuma ta balla masa harara tare da ƙoƙarin miƙewa. Sai dai yanda rigar tai mata masifar ɗam-ɗam a jikin yasa sai da tai ƙoƙarin dafa kujera. Fuska ya sake tamkewa da miƙo mata hijjabin. Batare da ya bata damar cewa wani abu ba duk da ya fahimci akwai abin faɗar a bakinta ya tareta da faɗin, “Haramunne matar aure ta fito a shiga mai bayyana ainahinta ga wasu, kai koda ma mara auren ce. Dan haka ki kiyaye inada kishi mai zafi. Wannan kuma ya zama first and last dan ban shirya rabarma kowanne sankaran ido ba, duk abinda akace nawa ne to nawa ɗinne ni kaɗai koda bana ra’ayinsa”.
Tuni wani irin tuƙuƙin takaici ya maƙure maƙoshin Lulu. Cikin kaushin murya da jifansa da wani malalacin kallon sama da ƙasa ta ce, “Kai a matsayin wa? Da ka isa hanani yin abinda yake ra’ayina!”.
“Ni a mijinki da ya biya sadakinsa”. Ya bata amsa cike da gadara da kaushi ga idanunsa da ya wani tsatstsareta da su kamar zai cinyeta.
Rasa abin faɗa dan takaicin da ya ƙulleta ya sata faɗin, “Mtsoww! To baka isa ba. Kayi tsararo Shash…..”
Bata kai ƙarshe ba ya tareta da faɗin, “To ke da kike jin kin isa ki sake sakawar ki fito ɗin zan tabbatar miki isar tawa kuwa.” ya ƙare magana yana jefa mata hijjab ɗin a saman cinya ya maida hankalinsa ga cire ruwan da ake ƙara masa dan ya ƙare. Mamaki ne, ko takaici, ko tsoro ne ya saka Lulu yin sagade tana kallonsa oho itama bata gama tantancewa ba. Idanunta sunyi masifar kaɗawa ga tarin masifar da take tattarowa na mata kai kawo a ƙirji. Ƙarasa miƙewa tai tana hucin bala’i, hakan yasa hijjabin ya faɗi ƙasa. Shima miƙewar yay duk da baya jin ƙarfin jikinsa, sai kawai ganinsa tai a jikin ƙofa yana saka mata key”.
“Kai wai mika ɗauki kanka ne?”.
“Duk yanda zuciyarki ta baki”.
“Mtsoww banda lokacin ka ban hanya na wuce”
“Idan kinbi abinda nace kenan. Saɓanin hakan na nufin cigaba da zama a ɗakin nan matsayin kinzo ke nan”.
“Mtsoww kana buƙatar ganin likita. Wlhy kaban hanya kona illataka”.
“Muyima juna illa dai. Dan wlhy idan kinga kin bar ɗakin nan to kin saka hijjab kuwa. In ko ba haka ba kimayi kiran waya gida tun yanzu a fara tattara miki kayanki a aiko miki”. Ya na gama faɗa ya bar wajen ƙofar yana zira keys ɗin cikin aljihun 3 quarter ɗinsa, sai ma ya shige toilet abinsa. Karo na biyu kenan da take jin an mata wulaƙanci mafi muni, randa ya kaita dawanau da kuma yau. Wai ita illiterate drivern nan nata zai ce ma sai ta saka hijjab sannan ta fita a ɗakinsa. Uncle You duk ya ja mata wannan rainin da tozarcin. In ba haka na velleger ɗin nan ko’a hanya yama isheta kallo ne bare har ya kalla cikin idonta wai ya bata umarni. Lallai dole ne ma wannan drama ɗin ya tsaya a haka. Dan bazata iya wannan auren contract ɗin ba kuwa…..
Motsin fitowarsa ya katse mata tunani. Ta buɗe idanunta da suka gama kaɗewa da ɓacin rai ta ɗan bisa da kallo. (Ƙaton banza) ta faɗa a zuciyarta tana mai kauda idanun nata da ga kansa. Saman katifarsa ya koma ya zauna, jug ɗin kununsa ya buɗe ya zuba a cup, sai kuma yasa sugar kaɗan da madara ya juya. Jan jikinsa yay baya ya zauna da ƙyau ya fara shan abunsa hankali kwance tare da ɗaukar wayar tasa ya fara sana’ar buga game ɗin ball tamkar ma ya manta da ita ne a ɗakin.
Fiitt yaji an warce wayar. Sai ya ɗago a ɗan zabure ya kalleta yana wani ɗan buɗe baki. Harara ta watsa masa kai kace Luulu eyes ɗin nata zasu zubo ƙasa ne. Kansa ya shafa yana wani ƙasa-ƙasa da nasa idanun. “Madam ni fa hararar nan tana sani tunanin kamar nayi wani abu, gaskiya in dai ana son a rabu lafiya to a daina, kin san abinka da ba sabin ba tuzuru da mata”. Ya ɗan sake ɗago ido ya kalletan sai kuma ya maidasu ƙasa kamar mai jin kunya.
Iya matuƙar kunnuwa kam Lulu ta kai maƙurar kunnuwa. (Mi wannan abin yake nufi?) Ta ayyana a zuciyarta, tsaf kuwa ta fahimtar da ita inda ya dosa. Wani irin waro idanu tai da faɗin, “What! Wait! Wait! Wai mi ma kake nufi?!”. Tsabar yanda take jin masifa da ɓacin rai takaicinsa jikinta har wani tsuma yake yi. Ya samu yanda yake so, dan kuwa ta kunnun fiye ma da yanda yake buƙatar. Idanun ya sake ɗagowa ya kalleta cikin son sake kaita maƙura ya ce, “Ni fa Madam ina jin kunya ne, amma idan kince na nuna miki a aikace sai na rufe ido, kema Please ba sai kin kalle ni ba sai ma mu kashe fitil……”
Wani irin mugun wawura ta kaima filos ɗin saman sofar ɗakin ta shiga jefa masa su ɗaya bayan ɗaya. Hannu ya sa ya dinga kare kansa. Ta ce, “Kai har ka isa ma yin wannan tunanin a kai na, har abada kai gaban abada ma ƙazamin yatsar hanunka ma bai isa zuwa ko kan veil ɗina ba ma illiterate velleger!”.
Dariyar da ke neman kufce masa ya keta faman dannewa. Dan muryarta har rawa ya ke na matsanancin takaicinsa, filos ɗin da ta gama loda masa a jiki da jifa ya shiga janyewa yana faɗin, “Ba sai kin ƙirƙiri hanyar maidani asibiti ba. Ni dai ina tsoratar miki ganin aikin jahilin baƙauyen nan a aikace. Dan kin san mu idan muka ɓalle ba’a iya taro mu saboda ƙazamin hannun nan da wahala idan zaiji bari fa. Sannan ki bar fassarani in da banje ba karki lalatama Ammah yaro tun ban tafasa ba ki ƙona ni Aliyu ba inda kike nufin na nufa ba”……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣9️⃣
__________________
___________________
…….Banza ta masa yanzun kam, dan ta tabbata ta cigaba da kulashi ƙarshenta fasa masa kai zatai kawai ya baje a ƙasa ko zata samu sassaucin tuƙuƙin da zuciyarta ke mata. Ta fara takaicin daɗewar Uncle Yousuf. Wayarta ta ɗauka tai kiransa, bugu biyu kuwa ya ɗaga. Muryarta na nuna alamar ɓacin ran da take ciki ta ce, “Papa wai kana ina?”. Ya fahimci ranta a ɓace ya ke, dan haka ya bata amsa da “Gani nan a hanya”.
“Papa bama ka nan?” ta faɗa a shagwaɓe, batare data jira cewarsa ba ta cigaba da faɗin, “ALLAH idan bakai sauri kazo ba zanma mutumin nan duk abinda zuciyata ke ayyana min na tsanesa”. Ƙitt ta yanke kiran kafin ma Uncle Yousuf ɗin ya samu damar cewa wani abu. Smart dariyarsa ya ke kwasa a zuciya, a zahiri kam ya fuske yana shan kununsa idonsa a tv. Ring ɗin wayarsa ya sashi kallar wayar dan tana a wajenta har yanzun. Itama wayar take kallo a yamutse cikin kuma harara. Sai dai bata da alamar bashi….
“Ni dai ki daina hararar min waya karta fashe ba kuma kuɗin sayen watace da ni ba gaskiya” yay maganar yana miƙo hannu ya ɗauka. Hararar da take ma wayar ta maida a kansa. Sai kuma tai ƙwafa dan tayi alƙawarin bazata sake tanka masa ba. Amma zai gane kurensa dan sai ta koya masa hankali. Kiran Uncle Yousuf ɗin yay back dan har wayar ta riga ta katse. Yana ɗagawa da ga can ya ce, “Aliyu su sameni waje ba sai na shigo ba anjima zan dawo in sha ALLAH”.
Cikin girmamawa ya amsa masa da to. Yana ajiye wayar ya dubi hijjab ɗin da ta jafar saman katifar sannan ya kalleta cikin komawa serious. “Kin shirya tafiyar ne ko nace masa ya je kawai ke kin tare?”.
“ALLAH ya isa tsakani na da kai”. Ta faɗa cikin tare masa numfashi. (Sai dai fa ALLAH ya isar) shima ya faɗa a zuciya. A zahiri kam sai ya ƙara ɗaukar hijjab ɗin ya miƙa mata baice komai ba. Sai da taja kusan minti ɗaya tana zabga masa muguwar harara sannan ta warce hijjab ɗin da ga hannunsa. Dan zuciyarta ta gama bata shawarar kawai ta saka ɗin ta bar ɗakin maganinsa kuma tayi da ga baya. Sannan ko mi Uncle Yousuf zai mata sai dai yayi yau ɗin nan sai an warware wannan auren dan taga raini ya ke son haddasa wa tsakanin ta da drivern ta. Baba kuwa zata fito ta faɗa masa gaskiya idan ta tubure dai ai dole ya barta. Karan farko a rayuwarta da ta saka hijjab bayan sakawar yin salla. Amma da sunan fita waje wai ta suturta jiki abune da bai taɓa faruwa ba koda da ga ɗakin barcinta ne zuwa falo kuwa. Yako mata matuƙar ƙyau duk da iyakarsa gwiwa, ga shi kuma mai hannu. Ƙamshin da yake na turaren wuta da aka turara masa yay matuƙar saka mata nutsuwa. Shima a hankali ya sauke wata sassanyar ajiyar zuciya acan ƙasan maƙoshi yana kallonta ƙasa-ƙasa. Sai dai yayi kamar ba kallon nata yake ba har sai da ta balla masa harara da faɗin, “Malam sai ka buɗe ai ko” cikin jan tsaki ta ƙare maganar.
Ɗagowa yay da ƙyau ya dubeta. Da ace zata yarda hoto zai mata, amma yasan son yin hakan wani sabon yaƙi ne kuma. Dan haka ya shanye maitarsa ta son yin hoton ya miƙe batare da yace komai ba ya nufi ƙofar. Koda ya buɗe ya bata hanya sai da ta zuba masa hararar nan dai da jan tsaki a kausashe ta ce, “Sai na koya maka hankali wlhy” sannan ta fice. Wani shegen murmushi ya saki da kai hannu ya shafo kansa yana binta da kallo. Sai da ya ga ta ɓacema ganinsa yay ƙaramar dariya da faɗin, “Mu koya ma juna dai ƴar madara” ya ƙarasa fitowa ya bita duk da baya jin ƙarfin jikinsa.
Tunda ta fito Uncle Yousuf yay wani sagade yana kallonta kamar wata sabuwar halitta. Aiko ta ƙara ƙullewa da haushi. Fuuu ta wuce ta buɗe motar ta shiga batare data tanka masa ba. Hannu ya kai ya tare bakinsa dan dariya ke neman kufce masa. Dai-dai nan Smart ya fito. Jin jina👍 yay masa da hannu yana wani kashe ido ɗaya. Smart yay murmushi kawai da ɗan shafa kai, cikin basarwa ya ce, “Uncle sannu da dawowa”.
Ƙasa-ƙasa Uncle Yousuf ya ce, “Ya akai ta saka hijjab?”.
Yanzu kam ƙaramar dariya Smart yayi, sai dai kafin yace wani abu ta katsesu da faɗin, “Papaaa!”. Yanda taja sunan kamar zatayi kuka ya sashi faɗin, “Sorry Baby gani nan zuwa”. Shi dai Smart dariya suke bashi ma. Buɗema Uncle Yousuf ɗin yay yana faɗin, “Deen ya samu Nasreen sai dai anjima na kawoshi ayi haƙuri”.
Cikin rashin damuwa Uncle Yousuf ya ce, “Oh to bara mu kama hanya. ALLAH ya ƙara lafiya you are the best Son”.
Murmushi Smart ya sake yi yana ɗan kai dubansa ga Lulu. Ta ɗauke kanta gefe irin ma bata buƙatar kallonsu ɗin nan. Godiya ya ƙarama Uncle Yousuf ya rufe motar yana matsawa gefe har sai da ya ga wucewarsu sannan ya koma cikin gidan yana dariyar ƴar balaja’un tasu. Dan ba yace tasa ba tunda ance masa anma fasa auren.. yana shiga ɗakin da gyalenta ya fara cin karo, da alama zamewa yay ya faɗi sanda take saka hijjab ɗin batare data sani ba itama. Hannu yasa ya ɗauka ya ɗan jujjuyashi, ƙamshi yake na fitar hankali dan Lulu bata san sassautama turare ba, gashi kuma da kusan kala bakwai take amfani. Iska ya ɗan furzar da buɗe drawer ɗinsa ya jefa gyalen sannan ya zo ya kwashe filos ɗin da ya sha jifa ya maida saman kujerar ya koma kan katifar ya kwanta shiru kamar mai barci…….
____________★
“Dama sai da na faɗa muku wannan yaron sam baiyi kama da driver ba amma kuka ƙi yarda. Yanzun ai kun yarda ko?”.
“Baita relax bafa munƙi yarda bane ba. Kawai dai a munce da kai akwai dai wani a ƙasa nunasa da sukai matsayin wanda zata aura. Kaima fa kasan shekara kusan uku kenan ina bibiyar rayuwar yarinyar nan, na sani ka sani bata tare da kowane namiji. Kuma yaron nan binciken mu ya nuna mana kwata-kwata bai wuce wata ɗaya ma da fara aiki tare da su ba. Kuma ƙaninsa ne ya kawosa ma matsayin driver gidan”.
“Humm Honorable karka yaudari kanka mana. Ka zauna kayi tunani da hankalinka dan ALLAH. Wata ɗaya da kaisa gidan matsayin driver, amma an ɗauki ƴa an bashi a jiya matsayin mata! Bafa babyn roba bace. Anya bai kamata ka tabbatar da akwai wata a ƙasa ba. Ni da kai duk mun san wanene Jiƙamshi ai bama buƙatar ƙarin bayani”.
Ido suka zuba masa su duka biyun. Maganganusa na musu kaikawo a zukata da tasiri ɗaya bayan ɗaya. Kamar an tsikari Hon. Misau ya zaburo yana karkaɗa hannu. “Gaskiya fa maganarka abar a duba ce Baita. Ko kun lura ma tsakanin Alh. Sulaiman da yaron akwai magana. Kun dai san waye Sulaiman Garko baya raina abokin gaba. Sannan a labarin da nake samu yanzun nan shima ɗan Sulaiman ma yaje massalacin cikin shirin auren yarinyar amma ya yanke jiki ya faɗin jin an ɗaura da wannan ɗin, shi kuma Sulaiman ɗin baije massalacin ba”.
“Eh to lallai akwai ƙullaliya a ƙasa”. Cewar Hon. Nakowa. Alh. Baita ne ya bashi amsa da “Babba ma kuwa. Dan tabbas Alh. Sulaiman nada tasa manufar na son yaronsa ya auri yarinyar duk da kuwa ɗiyar ƙanwarsa ce. Kuma shine sanadin auren uwar yarinyar da Isma’il ɗin”.
“Yess wannan gaskiya ne. Dan sai yanzu kuka dawo da ni cikin hankali na. Wai ya akai ma mu tun kafin yau muka kasa gane yarinyar nan ɗiyar Isma’il Jiƙamshi ce”.
“Lokaci ne bai yiba kawai sai yanzu”.
“Amma lokacin nan kam bai mana adalci ba. Sai dai inaga ya kamata muma muyi amfani da wanda ke kaɗawa a yanzun”.
“Kamar ya?”.
“Muna buƙatar zuwa duba ɗan Sulaiman asibiti, mu gyara abinda muka ɓata a baya sannan mu sabunta abota”.
Gaba ɗayansu kai suka shiga kaɗawa da gamsuwar abinda Hon. Nakowan ya faɗa. Dan haka suka miƙe a tare Alh. Baita na faɗin, “Da zafi-zafi akan bugi ƙarfe..”
★★……
Sai a safiyar yau aka samu dai-daituwar Tajuddeen yanda ya kamata. Faruwar hakan ta kawoma Alh. Sulaiman ƴar nutsuwar dawowar hankali cikin jikinsa. Yana matuƙar so da ƙaunar Tajuddeen. Dan shi kaɗai ne ɗansa tilo namiji. Sauran huɗun duk mata ne. Amaryarsa kuwa Abasiyya bata taɓa haihuwa ba har yanzu shekararsu kusan goma kenan kuma da aure. Dan haka ya ɗauki son duniya ya ɗorama Tajuddeen fiye da kowa a gidan. Gata yake masa na bala’i sai dai kasancewar mahaifiyarsa Hajiya Turai tsaye take kan tarbiyyar ƴaƴanta Tajuddeen ɗin bai lalace ba. A asibitin ya kwana, sai yanzu da Hajiya Turai ta zo dan ita gida ta koma ta kwana. Da ƙyar ta samu ya tafi gida dan yin wanka. Koda yaje gidan wayar da yake amfani da ita a kiran Smart ya lalubo. Yana ƙoƙarin kunnata amaryarsa ta shigo, ƙaramin tsaki yaja yanda bazataji ba yana ajiye wayar. Sannu da zuwa tai masa da tambayar mai jiki. Amsa mata yay a taƙaice da bata umarnin haɗa masa ruwan wanka. Duk yanda yake son kiran shegen yaron nan a ransa dole ya cije har sai da yay wankan ya tsakuri abincin da ta ajiye masa. Yana kammalawa ya ce ta kwashe ta bashi waje yana buƙatar hutawa. Baki ta taɓe da tattare kayan ta wuce, a ranta tana ƙun ƙunin takaicinsa da ga shi har matar tasa. Sai dai kuma ranta fes jin auren da suka so ƙullawa bai ƙullin ba, ta kumayi alƙawarin yin amfani da wannan damar ƙanwarta ta samu cikar burinta ita ma, amma dai zata basu lokaci har Tajuddeen ɗin ya samu lafiya…
Tana fita ya sakama ƙofar key, bedroom ɗinsa ya shige nan ma ya saka key sannan yay zaman ƙasaita cikin sofar ɗakin da waya a hannu…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣0️⃣
……..Idanunsa da ke lumshe ya buɗe a hankali ya saukesu akan wayarsa da ke ruri. Har wayar ta kusa tsinkewa yana kallon number da ake kiran nasa da ita, sai kuma yay murmushi yana mai cije gefen lip ɗinsa da ɗaukar wayar ya sa a hansfree tare da maida idanunsa ya lumshe, cikin nutsuwarsa da deep voice ɗin nan ya ce, “Assalamu alaikum. Ina magana da waye?”.
Alh. Sulaiman da ke huci da ga can ya ji wani irin takaici ya sake maƙure masa maƙoshi. A kausashe ya ce, “Da ubanka ne. Kai har kai ne zan kira ka ce min da waye?”.
Murmushi Smart ya saki mai bayyana sautin da har ya shiga cikin kunnen Alh. Sulaiman. Babu alamar ɗar a tare da shi ya ce, “Yes kaima uba ne kam. Dan koba komai na auri ɗiyar Sister ɗin ka. Uncle ina yini. Nafa gode da ƙyauta ALLAH ya saka da alkairinsa, insha ALLAH nan da wata tara zakuga tukuycin jika maybe ma sunanka zai ci. Sai dai bazanyi fatan ya gadoka ba, mai asalin sunan nake son ya gada da ƙyawawan halayensa nagartattu….”
“Yaro baka san wuta ba sai ka taka. Kana tunanin kai har karanka ya kai tsaiko kenan? Da har zan baka aiki ka koma gefe da tunanin cin dunduniyata! Wlhy ba kai ba hatta ahalinka sai sunyi nadamar kasancewarka a cikinsu. Ni Alh. Sulaiman Sufi Ado Garko sai na maida rayuwarka abar kwatancen da ko faɗar sunanka akai sai an tofar da yawu….”
Wata shashashar dariyar rainin wayo Smart ya saki cikin katsesa ya ce, “Da ace alƙalamin ƙaddarata a hannunka ya ke da tun kafin yau na kasance a ƙarƙashin inuwar tsoron cika bakinka. Sai dai kash kai baka isa ko dakatar da kaɗawar daƙiƙa ba na cikin ƙaddarata. Aliyu M. Idris Mawashi UBANGIJINSA kaɗai yake tsoro ba ɗan adam irinsa mai kashi da barci ba. Amma zan baka shawara idan ka shirya ka koma ka canja shiri, idan kuma baka fara ba ka ƙaro matakan shirin naka dan da kura kawai ake wasa a cikin kasuwa ZAKI sai kallo da ga nesa dan ko shafar jikinsa sai da dabara. Kamar yanda na faɗa maka nafi ƙarfinka kuma ni ba’amun barazana. Dan haka shawara ɗaya da zan baka ka goge tarihin alaƙar data taɓa alaƙantani da kai a baya, ka ɗauki sabuwar alaƙar zamantowarka suruki na sai mu amfana da tagomashi mutunta juna. Idan kuma ka ce a’a lallai zan cigaba da gara rayuwarka a tsakkiyar harabar gidan Alhaji Sufi Ado Garko fiye da yanda yara ke gara katantawar wasa a saman suminti. A yanzu bana buƙatar cewarka anan kaje kayi nazari. Na Barka lafiya sai nazo gasheka tare da AMARYAR ƘAMSHI bye Kawu”. Ya yanke wayar ƙittt. Kansa ya dafe yana wani irin furzar da huci a jajjere na ɓacin rai. Hannunsa ya kai saman goshinsa yana murzawa. Shi kam wace irin masifa ce wannan kuma ya shiga. Da ga wannan sai wancan. Sake furzar da iskar yay saboda abinda zuciyarsa ta ayyana masa cewar (Jarabawa ce).
Haukacewa Alhaji Sulaiman ya nema yi jin Smart ya yanke masa waya bayan ya gama yaɓa masa maganganu masu zafi. Cikin wani irin bahagon ɓacin rai ya shiga ƙoƙarin sake kiransa amma ana nuna masa busy alamar yayi blocking ɗinsa ma kenan. Dai-dai nan kiran Hajiya Turai mahaifiyar Tajuddeen ya shigo masa a ɗayar waya. Ɗagawa yay da sauri yana mai kaiwa kunnensa. Sai dai jin kukan data fashe da shi ya sashi zabura har da bugewa “Ke lafiya kuwa zaki ɗagamin hankali haka da kuka?”.
Cikin kuka ta ce Alhaji babu lafiya. Tajuddeen ya farka gashi nan yana aman jini, shike nan zamu rasas……” ai kusan da gudu ma ya fito da ga sashen nasa har yana neman faɗuwa. Ba ƙaramar tsorata maigadi yayi ba. Hakama drivern sa da yaronsa Malami. Da ƙyar ya iya sanar musu “Muje asibiti” ya buɗe gaban motar ta shiga batare da ya jira an buɗe masa ba. Dole suma suka shiga da hanzarinsu….
Tofa Tajuddeen yaya dai? Karfa ciwon son Lulun mu ya kasheka😔🚶.
___________________★★
A ɓangaren su Umma da aminiyarta masu tafiya garin Zuru da ƙyar ta samu Abba ya barta bayan ta lafta masa ƙaryar zuwa garin su duba Innarta, acewarta ƙanwarta tai kiranta da dare ta sanar mata jikin Innarsu ya motsa. Bai kawo komai a ransa ba tunda yasan Innar tasu dama jiyya take kusan shekara huɗu kenan. Ya jajanta mata da bata izninin tafiya dan haka ana sallame sallar asuba taima ƴan gidan sallama ta wuce. Duk da asubancin tafiyar da sukai basu iso garin Zuru ba sai bayan sallar azhar. Burinsu su kammala komai su koma garinsu Umma ɗin a yau su kwana. Sun koyi sa’ar samun Malam Na-zuru a gidan kamar ma su yay zaman jira kasancewar tun kan su taso sunyi kiransa sun sanar masa. Bayan gaisuwa da tambayar juna bayan rabuwa ya dubi Hajiya Naqiba dan ita kam bata rabo da zuwa inda yake har ma ta saba dan ta riga ta gama kama mijinta a hannu a sake take kamar akuyar fulani. Umma kam Abba bai kasance a ƙarƙashin ikon nata ba ɗari bisa ɗari shiyyasa zuwan ke mata wahala kai tsaye sai idan gagarumin abu ne ya faru.
“Hajjaju yau Aminiyar ki ta tuna damu kenan ko? Idan ban manta ba rabonta da nan kusan shekara uku kenan fa”. Cikin ƴar dariya Hajiya Naqiba ta ce, “Gaskiya za’ayi kam malam. Kasan ita akuyar ɗaure ce ganinta sai anyi sake ko tsautsayi ya gifta ta kufce”. Ta ƙare maganar tana kallon Umma. Dariya sukayi gaba ɗaya. Kafin Malam Na-zuru ya tsagaita da maida hankalinsa ga Umma yace, “Hajiya Yaha mike tafe da ke?”.
“Abubuwane da yawa kashi-kashi malam. Sai dai mafi girma a cikinsu aikin yaron nan ne mai shegen taurin kai ya ke neman buɗe min wlhy….”
“Tofa badai yaro mai tamaula ba ko?”.
“Wlhy shi kuwa malam. Dan jiya-jiya aka ɗaura masa aure da ƴar wani hamshaƙin attajiri”.
“Aure kuma? Ya akai haka ta faru Hajiya? Kina ina akai wannan babbar ta’asa bayan kin san da ƙyar muka samu yaron nan ya shiga hannun mu? Wannan kuma yana a cikin babban abinda muka ƙullesa da shi fa”.
“Wlhy malam nima ban san yaya akai hakan ta faru ba. Sai dai na lura tsabar munafunci ne na ubansu ya sa aka rufe mana komai sai ɗaurin aure kawai mukaji bayan an riga an ɗauro. Malam ka taimakeni dan ALLAH. Kai kanka ka sanar min yaron nan yanada taurari masu ƙarfin gaske da zasu iya disashe kaf ƴaƴan gidan nan ya zam babu hasken wanda ake gani sai shi, bayan kai malamai kusan huɗu sun sanar min hakan wasu ma sun kasa aiki a kansa sai kai ne da kayi akaci nasara. Gashi kuwa na fara gani dan aure fa akai masa, kuma da ƴar Alhaji Isma’il Jiƙamshi, wannan abu ya hanani samun barci sam a daren jiya”.
“Tirƙashi! Dolene ki kasa barci. Dan aurensa na ɗaya da ga cikin abinda muka ƙulle masa har sai ya tsufa a haka ta yanda babu mai ɗaukar ƴa ya bashi. Ba ƙaramin duka a ciki mijin nan yay mana ba gaskiya. Dan yaron nan yanada ƙarfin nacin ibada shiyyasa muka jima muna aiki yana tafiya a iska, na ƙarshen nan ma da ƙyar kina gani muka samu ya haushi da taimakon anfani da gashin mahaifansa da nashi…..”
“Na sani Malam, dan ALLAH ka taimakeni wannan aure ya watse kafin ma cikar sati ɗaya na tarewar wannan yarinya. Sannan a matse minsu waje guda su rasa gabas su rasa yamma akan wajen da zai zauna da abinda zasuyi hidimar biki. A sakama duk danginta tsanarsa a zuciya hatta da jaririn yaro. A birkitamin lissafin yarinyar ta ce bata son sa”.
“Aikin nan yana da wahala Yahanasu. Amma dai zaɓi ɗaya anan mu gwada mu gani”. Ya ƙare maganar da ajiye mata tazbaharsa gabanta. Da ƙyar ta iya tsaida nutsuwarta wajen ɗaukar ɗiyan tazbahar ɗaya ta miƙa masa. Amsa yay ya duba ya sake ajiye mata yace ta ɗauka. Sai da sukai haka sau uku sannan ya kalleta cikin jinjina kansa. “Gaskiya akwai babban aiki a gareki. Dan gaba ɗaya fa an riga an lalata aikin sai kaɗan ne bai bar jikinsa ba. Wanda kuma ya ƙulla wannan auren mutum ne mai nasibi matuƙa shima, dan komai yayisa ne da hikima kasancewar ya fahimci akwai ɓoyayyen al’amari akan rayuwar yaron……”
“Kenan babu yanda za’ai malam? Sannan waye shi wannan matsiyacin da ke tare da shi haka ba sani ba tun da wuri?”. Umma ta faɗa kamar zatayi kuka. Malam Na-zuru yay gyaran murya yana gyara zama. “Baza’a rasa yanda za’aiba kam. Sai dai dole za’a canja taku kuma. Shi wannan mutumin da kike tambaya yanada alaƙa da yarinyar matuƙa, sannan yana ƙaunar yaron da zuciya ɗaya, mutum ne kuma mai wayo da hikima gaskiya. Samun nasara a kansa kuma shima sai munyi yaƙi na gaske. Amma ita matar da aka ɗaura masa auren da ita mu maida akalar aikin namu ta hanyarta kawai inaga hakan zai taimaka mana”.
“To amma malam matar da ba’a bukatar ma ta tare miye amfanin kafa harsashin aiki kanta?”. Hajiya Naqiba ce yanzu tai masa tambayar dan Umma dai damuwar jin labarin waye Uncle Yousuf ya hanata magana ma. Amsa ya bata da faɗin, “Gaskiya in har kuna son cimma burinku akan yaron nan dole sai anbi ta hanyar ita wannan yarinya. Hakan na nufin kuma dole sai ta tare da shi sannan komai mu bisa a sannu…..”
Da sauri Umma ta ce, “Malam kana nufin ma har sai ya kusanceta a shimfiɗa kenan?”.
“A’a ba wannan nake nufi ba. Ko tarewa a gidansa tai matsayin mata to ya wadatar damu. Dan muna buƙatar kayan da aka kawota gidansa da shi a ranar, da wanda shi kuma zai shiga gareta da su. Sauran aikin ya rage namu mukuma”.
Jimmm Umma tai alamar tunani kafin ta sauke nannauyar ajiyar zuciya da faɗin, “Shike nan malam zanyi wannan ƙoƙarin. Sai kuma akan kishiyoyin nawa ina son a sabunta min aiki musamman uwar yaron nan. Dan na tsaneta fiye da kowa a gidan nan. Bana son koda ganinta matsiyaciyar. Yanda ta saka katanga tsakanina da masoyina har sai da ta fara zama matsayin matarsa na tsawon shekaru kafin ya kalleni bisa tirsasawar iyaye, wlhy itama sai na gunzuga mata baƙin cikin da har ta mutu bazata fita a cikinsa ba.”
“Burinki zai cika kuwa. Mudai je zuwa mataki-mataki zaki sha mamaki”.
Sosai farin ciki ya mamaye Umma, ta cigaba da zayyano ma Malam Na-zuru duk yanda take buƙata akan Ammah da zuri’arta. Suma sauran matan kowacce da kalar nata shirin da take so ai mata. Sai matar ɗanta Salim da itama ke neman zame mata ƙarfen ƙafa akan janye mata ra’ayin Salim ɗin. Basu dai baro garin Zuru ba sai bayan la’asar, a hakan ma ɗan basu tsaya yin koma ba. Sun jigatu kam gwargwadon iko sai kusan goma sha ɗaya na dare suka iso garin su Umma da nufin duba mahaifiyar Tata su kwana…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣1️⃣
………Tunda suka baro gidan babu abinda Lulu keyi sai haɗiyar zuciya. Ko sau ɗaya bata tankama hirar da Uncle Yousuf ke mata ba, hijjab nema da ya tambayeta ina ta samo cikin takaicin da har yanzu yaƙi sakar mata maƙoshi ta amsa masa da, “Uncle You mutumin nan fa ni bazan tare ba na fasa ko zaman wata ɗayan. Shiko dai yanata danne dariyarsa har suka iso gida. Sai da yay parking ya dubeta cikin nutsuwa ya ce, “Saboda mi basai kin tare ba?”.
“Ni dai kawai nama fasa. Dama na gaya maka mutumin nan baida mutunci, to kaga tun kafin ma na fara shuka masa nawa kalar rashin mutuncin kawai mu tsaya iya hakan”.
“To banƙi ta taki ba, amma yaya kike tunanin duniya da Baba zasu kalla al’amarin? Dan Baba fa zai iya ɗaukar zafin da bamu taɓa zato ko tsammani ba. Ni dai da zakiji shawarata anan ki cigaba da kwantar da hankalinki ayi komai a yanda aka tsarashi. Shima kuma mu bisa a sannu a rabu lafiya batare da kowa yaji ko ya gani ba. Dama jira nake ya sake samun lafiya yazo muyi magana ma ta fahimta ok”.
Sosai yanda Uncle ɗin nata ke mata magana cikin kulawa da sanyi ya sata jin bazata iya bijire masa ba. Dan haka ta jinjina kanta tana sauke tagwayen ajiyar zuciya ta ce, “Shike nan Papa. Amma dan ALLAH ka masa magana ya kama kansa”.
“Zan masa kar ki damu”.
Ya bata amsa cike da kulawa. Wata ajiyar zuciyar ta sake saki sannan suka fita. Da ƙyar Uncle Yousuf ya iya danne dariyarsa shi dai yana binta da kallo, tausayi take bashi, ba kuma ya ganin kowa da laifi sama da Daddy, ya raunana rayuwar yarinyar matuƙa da sunan soyayya, ya kasa fahimtar tarbiyyar uwa ga ƴaƴa daban take da komai a wannan rayuwar musamman ma ɗiya mace, amma sam Mawaddat bata samu ba, shiyyasa abubuwa masu muhimmanci ma duk bata sani ba kuma bata ganesu da yaren fahimta…..
Koda ta shiga gidan ma aunty Saliha dake yanke ma Ra’is farce a falo sakin baki tai kawai tana kallonta. Ai ko sai ta sake tunzura fuuu aka shige ɗaki. Dai-dai nan Uncle Yousuf ya shigo shima. Da hannu ta nuna masa bayan Lulu. “Miya kunna ƴar taka? Ga shi naga an dawo da hijjab?”.
Ƙaramar dariya ya saki yana kaiwa zaune. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Aikin surukinki ne”.
“Woow dan ALLAH fa?”.
“Sosai”.
Ya faɗa cikin gyaɗa kai da lumshe ido abin dariya. Sai kuma ya nuna mata Ra’is da ido. Murmushinta ne ya ƙara faɗaɗa. Sai dai bata sake cewa komai ba….
★★……
A matuƙar tashin hankali Alh. Sulaiman ya isa asibiti. Sai yay dai-dai da isar su Hon. Nakowa da sukaje duba Tajuddeen. Shi baima lura da su ba. Sai dai ganin yanda ya fita a mota a rikice yay cikin asibitin ya sa su tambayar drivern sa ba’asi. Shima ba sani yay ba. Sai dai ya tabbatar musu maybe jikin Tajuddeen ɗin ne. Jin haka suma sukai cikin asibin dan dama tafiyar sun yita a sirrance ne shiyyasa babu wani tare da su sai su ukun. Sun iske kam abubuwa sun ƙwaɓe matuƙa, Hajiya Turai da Alh. Sulaiman rungume da Tajuddeen suna kuka. Sam sunma ƙi bari likitocin suyi aikinsu. Hakan ya bama su Alh. Baita yin ruwa da tsaki akan komai. Dan take anan suka shiga ciku-cikun ganin amma fita da Tajuddeen a ƙasar ta wayoyi duk da sun san shima Alh. Sulaiman ɗin duk yana da wannan alfarmar. To da ace lafiya lafiya ne ko jirgi sukutum mahaifinsa yay niyyar nema dan akai Tajuddeen wata ƙasa neman lafiya hakan ba komai bane. Dan da gasken gaske Alhji Sufi Ado Garko ya tara dukiya irin wadda shi kansa bai san adadinta ba. Alhmdllh burinsu kam ya cika, dan zuwa yamma an kammala komai na fita da Tajuddeen, haka uwar da uban suka wuce batare da sun nema kowa a family ɗin ba. Ita kanta amaryarsa Hajiya Abasiyya sama-sama ya mata bayani lokacin da suka koma gida domin shiryawa……
★★★……
Duk wani abinda ke faruwa har barinsu ƙasar Alhaji Sufi Garko ya sani sarai. Sai dai yaƙi yin ko tari akan hakan dan ransa a ɓace yake matuƙa da ɗan nasa. Babu irin haƙurin da matarsa bata bashi ba amma bai saurareta ba. Sai ma gargaɗin karta sake masa maganar Sulaiman a gidan yay mata. Tare da balbale ta da masifar cewar duk wata fitina da ke a tsakanin ƴaƴansa ai itace tushenta. Dan sakacinta ne saboda kasancewarta mace mai masifar son ƴaƴa. Badan shi tsayayyen mutum bane da kaf ƴaƴansa zasu tashi ne a lalace cikin fanɗararriyar tarbiya. Dan tabbas Hajiya Attine bata tsawatarwa yaranta tun ma da ƙuruciya. Komai yaro ke so shi yake yi, ba’a isa kuma ace yay ba daidai ba sai ta kareshi. Yanzu haka akan auren nan na Mawaddat sai da ta haura sama sosai da mijin nata. A cewarta ai itama tanada hakki akan Mawaddat tunda itace ta haifi uwarta. Ita bata yarda Lulu ta auri talaka ba kamar yanda uwarta ta auri ubanta da ga ƙarshe suka kashe mata yarinya dan suci dukiya. Shiko kasancewarsa jarumi mai tsayawa a gidansa ya ce idan ta isa taje ta warware auren mana. Sun haura sama ƙololuwa koma ace har yanzun a saman suke, dan taso fita duba Tajuddeen nan ma yace idan ta fita a bakin aurenta. Wannan kalma ta matukar girgiza mata zuciya dan bata taɓa tunanin fita da ga bakin mijin nata da suka ɗauki tsahon shekaru kusan saba’in tare ba. Ta san kuma zai aikata dan shi baya magana biyu. Dole dai ta haƙura da fitar tunda suma yaran har ma da jikoki ya tabbatarma duk wanda yaje asibiti duba Tajuddeen sai ya koya masa darasin rayuwa…..
_______________★
A cikin gida koda Nasreen taje da Deen a wajen Mubarak suke jin baƙin da sukazo duba Smart ne sukazo da shi. Babu wanda ya damu da sanin da ga ina, duk da dai zuciya na raya musu ko dangin matar tasa ne. Dan yaron dai da ganinsa kasan ɗan gidan madara ne. Kuɓul-ƙubul da shi. Sai dai abinda ya birgesu da yaron yanda duk da ƙanƙantar shekarunsa sai da ya gaidasu. Fuskar Ammah da murmushi ta ɗaukesa ta ɗaura saman cinya tana tambayarsa sunansa. Yako bata amsa da cewar Deen shalelen aunty Luu.. shalelen aunty Luu da ga faɗa ya sakasu darawa, abinka kuma da yaro shi ko’a jikinsa, sai ma janye ra’ayinsa da Nasreen tayi suka kama wasansu batare da ya sake tunawa su Aunty Lu zasu iya tafiya su barsa anan ba. Bayan sallar azhar Smart ya shiga cikin gidan. Sunta jera masa sannu da yaya jiki? Dan sun barsa ne dama saboda maza da keta faman shigowa ƴan nan cikin anguwa dubashi tun safe. Zaune ya kai yana amsa musu da Alhmdllh. Yaji daɗin ganin Deen nata wasanshi, sannan koda aka zuba musu abinci shi da Nasreen babu wani janjeni yaron ya zauna sukaci. Shine ya sake musu bayanin daga inda yaron ya fito, sai dai ba gaya musu harda amaryarsa akazo ba. Anan ya ɗan sake shan kunun gyaɗa kaɗan ya kwanta a doguwar kujerar Ammah yana sauraren tsare-tsaren biki da suke tayi, dan shi sai yanzu ma yake jin wai aunty Bilkisu da Hawwah ashe sun tara masa uban kaya na lefe da suketa saye a hankali da shirin dama duk randa ya tashi aure sai dai a ƙarasa abinda ba’a rasa ba. Idanu kawai ya tsirama ƴan uwan nasa yana jin matuƙar ƙaunarsu a cikin ransa. Suko sunata dariya da tsokanarsa. Shima dole yay murmushi yana haɗiye abubuwa masu dama da ke a ransa. Anan ne Ammah ke masa bayanin shawarar da ta yanke akan inda zasu zauna. Sun gama shawara da ƙanwarta Sa’adah zasuyi magana da Abba a gyara masa gidan da suka gada kasancewar su biyu ne dama ke da shi ta ɓangarensu dan suma sunada ƴan uba. Sai yay zamansa, za’a tashi ƴan hayar gidan.
“A’a Ammah kar ayi haka. In dama ace babu kowa a gidan ne, amma bazan so saboda ni a tashi mutanen da ke a gida tsahon shekaru ba kuma a ƙurarren lokaci irin wannan. Kudai bani lokaci ina kan nazari in sha ALLAHU za’a sami mafita. Dan dama zance kodai a musu magana su kai tarewan zuwa sati biyu haka ko wata ɗaya”.
Ammah ce ta katsesa da faɗin, “A’a Hydar kar ai haka. Tunda mutanen nan sukace sati ɗayan kawai mu amsa ayi a wuce wajen. ALLAH shine zai rufama kowa asiri. Dan kaga dai a ɓangaren lefe Alhmdllh matsalarsa kamar ta ƙare zance. Ga dai Hawwah nan da Bilkisu zasu shiga kasuwa da kuɗin da ke hannunsu tun da sunyi alƙawarin dai sune zasu haɗa lefen nan. Ko a yanzu ma suturar da suka tara ɗin fa tafi arba’in tunda kowa na saye ta ɓangarensa. Gashi Alhamdullah duk manya ne kamar sun san inda auren naka zai faɗa dama. Kaga yanzu kam kokawarmu ai ta wajen da za’a zauna ne kawai sai kuma kai ɗan ɗinkunan da zakai amfani da shi na angwanci”.
“Kai Ammah ni sai nayi wani sabon ɗinki?”.
Hararar sa ta ɗan yi da faɗin, “Oh da haka kake son shiga angwancin. Haba Babangida, ai lokacin abu ayisa kaji. Kasan kuwa a irin farin cikin da nake ciki tsakanin jiya da yau. Ko auren su Maryam bai damuna kamar yanda zamanka babu mace ke cimun rai. Na gaji da jin gori da habaici akan zaman nan naka babu mace har ma da sheri. Amma Alhamdullah ga iyaka ALLAH ya kawo a gaɓar da bamuyi zato ba sai kuma muƙi nuna godiyarmu garesa.”
“Hakane Ammah. Amma ai inata sakaku wahala. Sam ba haka naso al’amarin nan yazo ba. Ban so ɗaura nauyin aurena a kanku ba, domin nine ya kamata nai muku hidima bawai ku kucigaba da min ba bayan tun ina ciki kuke min har zuwa yau ɗin nan”. Yanda yake maganar cikin damuwa ya sa Ammah sakin murmushi da miƙewa tana faɗin, “Shi komai lokaci ne da shi. Haƙuri akan jarabawa kuma cikar kamala da imanin ɗan Adam ne. Idan aka cigaba da jurewa duk komai zai cigaba da zama labari tamkar bai faru ba, ko a yanda auren nan ma yazo ai babbar aya ce. Fatana ni dai ka kasance da iyalinka fiye da yanda nake zatonka da tsammani. Ka kuma riƙe mutuncinka dan kar zuciyarka ta ɗora maka cewar dan su masu shi ne shikenan zaka zauna su zame maka rijiyar tatsar abin duniya. Babu ruwanka da dukiyarsu ka tashi ka nema na kanka ka ciyar da ƴarsu ka tufatar da ita da kare mata dukkan wani hakkinta da ke a kanka. Kar ka yarda ka bada wata ƙofa ta amsa da ga garesu da sunan wai kana auren ƴarsu. Duk da dai bana kokwanto a kanka Aliyu. Ina dai sake tunatar da kai ne dan dukiya shu’umar abuce mai shiga rai da jinin ɗan adam harma da ɓargo.”
Sosai nasihar mahaifiyar tasa ke ratsashi matuƙa. Tana ƙara masa ƙwarin gwiwa akan nasa ra’ayin kuma da ƙyakykyawar manufa………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣2️⃣
……Shirye-shiryen biki kam ya kankama ta kowanne ɓangare. Yayinda shima Abba ya goce batun tada mutane da ga gidan su Ammah a gyarama Smart. Yana ganin hakan zai zama su kuma an cuta musu. Gara dai kawai a kama masa haya na shekara biyu idan zai samu kafin aga abinda ALLAH zaiyi kuma. Ana cikin wannan lissafi sai ga Coach ɗin su Abdull-Hameed yazo da batun Smart ya amsa gidansa da ke anguwar sharaɗa ya zauna har sanda ALLAH zai hore masa nasa. A cewarsa wannan itace tasa gudummawar. Da farko dai Smart ƙin yarda yay, sai dai ya kafe akan zai biya kuɗin hayar gidan, sai da Coach ya nuna masa ɓacin ransa akai sosai harda faɗin ashe shine keta haukansa Smart ɗin bai ɗaukesa matsayin Yaya kamar yanda shi yake masa kallon ƙaninsa Ahmad ba, yay fushi zai tafiyarsa sai da ƙyar Smart ya bashi haƙuri ya tsaya suka tattauna. Da ga ƙarshe dai Abba ya ce an amshi gidan sukai godiya da sanyama Coach ɗin albarka dan ya jima yana ɗawainiya da Smart. Duk wani matakin nasara akan ball shine riƙe da hannun Smart ɗin. Dan tunda ya ga iya ƙwallo na Smart a wani wasan sada zumunta na makaranta da sukai sannan Smart na ss1 ya jashi jikinsa, tun ma suna ɗar-ɗar har suka saki jiki da juna ganin kowanne nada zuciya mai ƙyau. Kusan family ɗin su Ahmad sun san Smart sosai, haka suma family ɗin Smart sun san waye Ahmad da Abdull-Hameed a rayuwar Smart. Babu hanyar da Umma batabi na son ganin ta rabasu ba amma hakan ya gagareta shiyyasa ta tsani Coach matuƙa. Akwai lokacin da har sharri tai masu wai Coach kodai yana ɗabi’ar banza da Smart ne. Sai da Abba ya nuna mata asalin haukarsa a lokacin dan har saki ɗaya yay mata sannan ta dawo hankalinta tana bada haƙuri, da ga nan bata sake maimaitawa ba kuwa.
Smart yaje ya ga gida tare da Ahmad. Gidane madaidaici zaman mace ɗaya flat. Bedrooms uku biyu manya ɗaya ƙarami kowanne da toilet sai falo babba tare da dining, sai kitchen da store. Harabar gidan zai iya cin mota biyu zuwa uku. Ga flowers an zagaye ko’ina da suka ƙara ƙawatashi. Sabon fenti da gyare-gyare duk an masa, dan ana dawowa da ga ɗaurin auren Smart Coach ɗin ya nema masu aikin gidan aka fara. Dama ƴan hayane suka fita kusan watanni huɗu kenan kasancewar ALLAH ya hore musu suma sun gina nasu, shi kuma sai bai sake saka kowa ba a ciki ya ɗan fara masa gyara sai kuma ya watsar ya rufesa kawai. Sai da idanun Smart ya ciko da ƙwalla, dan a rayuwa yakan rasa mizai ma Coach ya iya kwatanta alkairan da yay masa ne koma yake a kan masa, ya jima yana ɗawainiya da shi kashi-kashi da shi kansa bai san adadi ba.
Bayan sun dawo suma su Aunty Bilkisu sukaje suka gano, Abba kuma da Ammah sai washe gari ya kaisu suma. Su Umma dai basu san hidimar da ake ba, summa koma gefe sun zuba ido suga wai yaya wasan zai ƙare ne. Dan ta aiwatar da ƴan abubuwan da malam Na-zuru ya bata yanzu jiran ranar tarewar amarya kawai take ta samu kayan da aka kawota da su da wanda Smart zai saka shima. Alhmdllh lefe ma ya haɗu tsaf, dan bayan ƙoƙarin su Hawwah suma dangin Ammah sun taka rawar gani, dama su mutanene masu haɗin kai matuƙa. Gashi kuma yanzu ne Ammah zata aurar da ɗa namiji kuma shi kaɗai tilo gareta. Hankalin su Umma da ya ɗan fara tashi ganin gudunmawar da keta shigowa mai jijjiga zukata da ga ƴan uwa da abokan arziƙi, dan ko kuɗi Smart ya samesu ba laifi. Ana saura kwanaki uku ya amsa kiran su Uncle Yousuf, dan rabonsa da gidan fa tun kafin a ɗaura aurensa da gimbiya. Aiki bai sake zuwa ba, dan itama dai Lulun Uncle Yousuf ya dakatar da ita fitar bisa wayon Aunty Saliha da ta ɗakko mai mata gyara tun daga Sudan da Marocco. Da farko tayi butsutsun nata na bata so Uncle Yousuf ya zauna ya tsarata tsaf a kwali dole tabi. Suma dai shirye-shirye suke na bikin ƴar gata, musamman ma Uncle Yousuf da Baba da Mommy da Aunty Saliha. Ya samu tarba ta muntunawa ga Mommy matsayin suriki garesu a yanzu. Duk da dama dai ita kam bata taɓa wulaƙantashi ba. Shima ya gaishesu cikin mutuntawa da girmamawa kamar yanda ya saba. Da ga haka suka fara tattauna abinda ya tarasu. Shiru yay yana sauraren Daddy da ke masa bayani akan takardun hannunsa. Ɗaya na gida da ya bashi halak malam ƙaton gaske anan cikin anguwar hotoro G.R.A ɗin upstairs ma, sai key na mota da takardunta itama sabuwa fil a ledarta, da zunzurutun kuɗi har naira miliyan ashirin, ya kuma zaɓi duk aikin da yake so ya nema masa. Tunda Daddy ya fara murmushi kawai Smart yake yi amma baice komai ba. Shima dai Uncle Yousuf da Mommy basu ce komai ba dama.
A hankali Smart ya girgiza ma Daddy da ke miƙo masa takardun da key ɗin motar kai. Cikin tausasa harshe da girmamawa ya ce, “Daddy kayi haƙuri bazan amsa komai da ga gareku ba ni. Na auri Mawaddat ne domin ALLAH da bautarsa. Na kuma muku alƙawarin riƙeta in sha ALLAHU da abinda ALLAH ya azurtani da shi, bazaku taɓa dana sani da ni ba. A yanzu haka inada inda zan ajiyeta, batun neman aiki kuma insha ALLAH shima zan nema abinyi da kaina, hakan zai fi ƙaramin himma da sanin muhimmancin abinda na samu ɗin. Idan nayi ba dai-dai ba a gafarceni dan ALLAH”.
Tsittt falon yay tamkar ruwa ya cinye kowa. Bakaji komai sai sautin ƙarar ac da ke aiki. Murmushi sosai Mommy da Uncle Yousuf keyi ƙasa-ƙasa. Yayinda Daddy yay wani sansarakwai da shi yana kallon Smart cike da mamaki da al’ajab. Kaba mutum irin wannan dukiyar amma ya nuna maka bai buƙata, matashin saurayi kuma da ayanzu yake fafutukar gina rayuwarsa. Da ƙyar ya iya jan numfashi har sannan idanun nasa dai akan Smart. Ya ce, “Aliyu ban baka wannan abubuwan ba dan wataran ka maido min da madadinsu. Na baka ne saboda kaima yanzu matsayin ɗa kake amsawa a garemu, fatanmu kawai ka riƙe mana Mawaddat cikin aminci da amana”.
“In sha ALLAHU Daddy zan cika alkawarin riƙeta, koba komai nima inada ƴan uwa mata, bazan so na tsinci rayuwarsu cikin aƙubar zaman aure ba. Zanyi iya ƙoƙarina kamar yanda MANZON ALLAH (S. A.W) ya koyar da mu murayu a gidajen auren mu”.
Magana Daddy ya ƙara yunƙurowa zai yi cikin ɗan jin haushi-haushi, amma sai Uncle Yousuf yay saurin taresa yana girgiza masa kai da faɗin, “Shike nan Aliyu mun gode da wannan karamcin naka. Dama mu ai hakan muke son ji da ga gareka. Zamu cigaba da muku fatan alkairi dana zama lafiya. ALLAH ya baku ikon sauke hakkin juna. Ga waɗan nan katunan Baba ya ce a baka. Sai dai yace a faɗa maka kayi haƙuri baiyi shawara da kai ba wajen haɗa wannan dinner, yaso yin hakan sai uziri mai girma ya taso masa dan yanzu haka ma yana Abuja. Muma a madadinsa muna sake neman afuwarka da roƙon kayi haƙuri ya haɗa dinner ɗin ne sakamakon yanda ɗaurin auren ya kasance ga kuma mutane da yawa ya cancanci suzo”.
Ɗan murmushi kawai Smart yayi, duk da harga ALLAH shi a tsarinsa babu batun waɗan nan bidi’oin, amma yana jin nauyin Baba da Uncle Yousuf ɗin. Dan haka ya amsa katunan yace ba komai abin ƴan awoyine ai. Da ga haka yay musu sallama ya wuce da sanar musu baƙi na zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Daddy dai bai tanka ba, hasalima ransa a ɓace yake. Taya zai haifi yarinya, ya raineta tsawon shekara ashirin da huɗu. Rana ɗaya tak wani ya nuna masa iko akan al’amuranta. Idan bai amshi waɗan nan abubuwan daya bashi ba taya zai riƙe masa yarinya da daraja kamarr yanda ya raini abarsa. Sosai Mommy ta fahimci yanda Daddy ke cika da batsewa, dan haka ta miƙe tana cema Uncle Yousuf bari taje tai waya da su Hajiya Aysha da su Aunty Saliha suzo a tsara abinda za’a tarbi baƙin da Smart ɗin ya ce zasu zo gobe. Cikin murmushi da barkwanci Uncle Yousuf ya ce, “Umm bafa sabun ba zamu aurar da ƴar farko a gida”. Dariya ta fita tanayi. Shima yana tasa. Tana gama ficewa Daddy ya miƙe a zafafe.
“Kai Yousuf bazai yiwu ba. Shiyyasa tun farko nace maka yaron nan zai iya bamu matsala dan na fahimci gadararre ne shi mai girman kai. Taya zan bashi abinda zai inganta rayuwarsa da ma ta duk zuri’arsa darajar ƴata zata shiga cikinsu amma ya nunamin shi yafi ƙarfin hakan bayan baida komai. To gaskiya ayi komai a rubuce wata ɗayan daka ambata ya sakamin yarinya ta kawai……” Haka ya cigaba da zazzaga masifa ko haɗiyar yawu bayayi. Shi dai Uncle Yousuf na zaune kawai yana kallonsa har yayi ya gama. Baice komai ba, sai ma ya tashi tsam ya fice a falon yay tafiyarsa ya bar Daddy da sakin baki yana kallonsa………✍️
(Uncle You kaima fa ɗan manni ne wlhy🤣).
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣3️⃣
…….A ɓangaren Smart sosai abinda ya farun ya dinga cimasa rai. Amma haka ya danne bai sanarma kowa ba yama kashe wayarsa dan kar wani tsakanin su Daddy yace zai sake kiransa akan batun. Bayan ya koma gida ya shiga ciki gaida Ammah su Hawwah suka buɗe masa lefe ya gani. Set guda na akwati mai biyar, sai ƙwara biyu daban da Abba ya saya da kaya a ciki suma matsayin kayan sa rana. Kaya kam sunyi sai dai maƙiyi, ga shi kuma duk manyan atamfofi da lasses hakama shaddoji da dogayen riguna dai-dai ƙarfin mai rufin asiri dai. Sosai Aunty Bilkisu da Hawwah suka taka rawar gani, dama sunyi alƙawarin duk randa ɗan uwan nasu tilo ɗaya ya tashi yin aure sai sun nuna bajintar da zata girgiza jama’ar gidan nasu kowa ya tabbatar da shi ɗan gata ne. Aiko sun girgiza ɗin, dan ko gidan su ya girgiza matuƙa da ganin wannan lefe da ba’a taɓa tunanin gani ba, sai su Umma suka shiga yada habaicin wai sai dai in iyayen yarinyar ne suka haɗa lefen, da ga Ammah har ƴaƴanta babu wanda yay ko tari har sukaci suka tsire. Gyalillan ciki kaf ya kwashe yabar guda uku, da mamaki su Aunty Bilkisu ke kallonsa, duk da ya lura da hakan baice komai ba ya dubi Maryam ya ce, “Bani saƙon dana baki ajiya”. Tashi tai tana murmushi ta shiga bedroom ɗinsu. Babu jimawa ta dawo da leda babba ta miƙa masa. Amsa yay ya miƙama aunty Bilkisu da faɗin, “Ku saka waɗan nan a kayan, wannan kubarta har sai tazo na bata da kaina. Aunty Bilkisu zatayi magana Ammah ta katseta da faɗin, “Kumasa yanda yake so ɗin kawai tunda baku san dalilinsa ba”. Su masu biyayyane ga umarnin mahaifiyarsu, dan haka babu wanda ya sake magana aka loda hijjabai da suka sha guga har guda goma ciff cikin akwati….
Washe gari alhamis aka kai lefe, ba wani gayya akai ba. Umma ne da Aunty Amarya, sai Aunty Bilkisu da Inna Mariya. Da wata gwaggon su mai suna Jamila. Sai matan maƙwaftansu su biyu. Ahmad ne ya kaisu da motarsa, sunko samu tarba irin wadda basuyi zato ba. Dan su Mommy da su Aunty Saliha sun nuna karamci mai ban mamaki. Ga gida cike masha ALLAH iyalan gidan Baba suma sun zazzo. Sosai suma kansu su Mommyn sukasha mamakin wannan lefe, dan gaskiya basuyi zato ko tsammani ba. Abu a cikin kwana shida haka. Kai da mamaki. Ga kaya babu na kushewa sai san barka. Harda kuɗin ɗinki, sai dai basu amshi kuɗin ɗinkin ba dai. Su Umma fa sun girgiza matuƙa, dan ganin gidan su Lulun ya ƙara tayar musu da hankali da sake tabbatarwa eh lallai Smart ya shiga inda akafi ƙarfinsa, dan yanda mutanen keda wannan irin dukiya sai dai idan asiri ne yay tasiri, yo inba asiri ba ƴar data tashi a wannan gidan ce zata auri ɗan talakawa kamar Smart. Ammah dai tasan tsiyar data yi ɗan nata ya auri yarinyar nan. Duk wannan abu dake faruwa amarya bata sani ba, tana gidan Aunty Saliha data turketa ana mata gyaran jiki na fitar hankali. Dan ta ƙara wani irin fresh da ita, damuwarta ɗaya kayan shaye-shayen ta da bata samu. Dan a jiya har kuka tayi ita kaɗai a bayi saboda buƙatar son sha da takeyi amma babu dama. Tsoffin nan da aka kawo mata sunbi sun tare ko’ina basa barinta ko motsin kirki. Gasu da ihu da tace zata musu gardama suke rufeta da kwakwazo dole take zama suyi yanda suke so da ita. Sai dai ita kanta tasan ta canja. Dan fatan ta ko daga nesa ka hangota kasan ta ƙara karɓar sunnonin gyara. Ga wani almurin ƙamshi mai ratsa zuciyar mai shaƙa. Ita kanta ƙamshin ne ma ke tafiya da imanin ta shiyyasa wani lokacin take ragama tsoffin ta haƙura su zauna.
Bayan wucewar ƴan kawo lefe da aka cika da sha tara ta arziƙi suma su Aunty Saliha suka nufi gidan da za’a kai Mawaddat ɗin domin raka Company da Uncle Yousuf ya bama kwangilar shirya mata kaya. Su kansu gidan ya birgesu yanda yake cif-cif abinsa. Duk da nasu ya ninka shi sau biyar girma da ƙyau, shima wannan ɗin nada nashi kalar sirrin ƙyau ɗin da yanayin shiga rai. Bayan Company sun kammala aune-aunensu su Aunty Saliha suka dawo gida suka barsu suyi aikinsu. Dan gidajen biyu sun fara cika da ƴan uwa na jiƙamshi da abokan arziki musamman na tsohuwan anguwar da su ka rayu tun suna ƙanana kasancewar mutanen da da zuminci ga shi kuma Aunty Saliha ma ƴar canne. Anan gidan su Smart ma dai an dawo da labari mai daɗi na tarbar da suka samu da karramawa. Yayinda Umma keta faman haɗiyar zuciya, data samu abokin gulma kuwa tace “Anya yarin nan ba asiri yay ma mutanen ba kuwa? To wannan haba rawa har ina. Ga mutane a jiƙe cikin kogin dukiya amma sunama waɗan nan ɗan abinda muka kai haba rawa haka”. Wasu idan tace musu hakan sukan kulata, wasu ko su gwaleta. Wannan kai lefe ya sake yayata sanin ƴar wa Smart ya aura a anguwar, dan dannan fa masu hassada da masu taya murna aka kafa teburan kace nace kowa na faɗar albarkacin bakinsa. Oho shi baima san sunai ba. Yana can yana nashi ƙoƙarin na ganin walimar da suma suka shirya anan gidan a gobe idan ALLAH ya kai mu juma’a ta tafi dai-dai. Ga kuma can gidan da Company ke saka kaya dole suka raba hankalinsu biyu shi da Ahmad da wasu tsirarun abokansa da basa fushi da shi duk yanda yake sharesu a baya. Harda Sa’ad mijin Hawwah.
Zuwa washe gari suma fa nan gidan ya cika da dangi, musamman ma dangin Ammah kai harma dana Abban da kuma nasu aunty Amarya, ga ƴaƴan gidan duka dai duk sun hallara ƙwai da kwarkwata. Duk da wasunsu aikinsu tsogumi ne da kushe kamar yanda iyayensu keyi. Bayan an sakko massalacin juma’a aka fara walima da aka gayyato manyan malamai da zasu kwarara wa’azi. Abin mamaki sai ga gayyara Alhaji Sufi Ado Garko a wajen da na Uncle Yousuf da wasu a cikin mata ƴan biki. daddy dai baizo ba, Mommy ma saboda baƙi doke ta haƙura, sai Aunty Saliha ce ta jagoranci matan da akazo da su sai yazam kamar an raba Mommy nacan ita tana nan. Sosai suma gidan su Smart ɗin suka maida alkairi da alkairi, dan sun musu tarba ta mutuntawa duk da ba’asan da zuwansu ba. Amarya dai banda ita, tana can ana mata ƙunshi bayan Uncle Yousuf ya mata filla-filla da masifa yau dan da taƙi yarda ayi, tun yana lallashinta yaga taƙi saurarensa sai ma sake tuburewa take akan itafa babu inda zataje ya sashi yau buɗe mata wuta irin wanda bata taɓa gani daga garesa ba, dan har rantsuwar marinta yay idan bata shiga hankalinta ba. Ga wayoyinta dama ya ƙwace kusan kwana uku kenan. Dole dai ta haƙura ana can ana yarara mata wani lalle na nunama sa’a da tsara. Sosai walima tai matuƙar ƙayatarwa. Ango yasha ƙyau cikin dakakkiyar shadda sai kaiƙo take. Tana ɗaya daga cikin ɗinkunan da Abba yay masa har kala biyar domin fitar biki, sai kuma ga Ahmad da nasa kayan mamakin a safiyar yau da ƙaton akwati guda da ɗinkakkun kaya masu ƙyau har kala ashirin shima matsayin tasa gudummawar. Har ƙwalla Smart yayi a ɓoye na godiya ga UBANGIJI da ya rufa asirinsa. Dan baiyi zato ko tsammanin haka ba shikam. Walima ta matuƙar ƙayatarwa ga armashi data ƙara dalilin zuwan dattijon ƙwarai Alhaji Sufi Ado Garko da tawagarsa ta ƴan siyasa har da gwamna da yazo daga baya shi. Aifa sai gashi ƴan jarida sunyi caa anata ɗaukar rahotanni, labaran daran juma’ar nan sai gashi ya zo harda wannan taron walima darajar zuwan su Gwamna wajen. Ranar fa anguwar fagge kamar zata fashe (Kar wani ɗan fagge naji yayi magana😏🥱😂). Duk da babu inda abincin da aka tanada yajema mutane kasancewar abin ya zarce yanda aka tsarashi mutane basu damu ba. Ko’a tv kaga kanka ai ka more🤣 (Su Smart an auri ƴar gidan madara an samu promotion 😜). Tarofa yayi taro fiye da zato, dan da ƙyar aka tashi bayan sallar magrib. Dauriya kawai ango yake da ambaton addu’oi a cikin ransa dan gabansa haka kawai yake ta faɗuwa. Ga ciwon kai ƙasa-ƙasa dake nuƙurƙusarsa. Haka dai yayta dauriya bawan ALLAH dan manyan mutanen nan sai da Uncle Ameen ya kama hannunsa ya kaisa gaban kowanne suka gaisa. Da yawansu sun yaba da nutsuwar yaron, har wasun su najin sha’awar yin koyi da wannan al’amarin aure da a yanzu al’ummar mu suka daina. Da wahala kaga ɗan masu kuɗi ma ya aure mace ƴar talaka balle wannan ace namiji ne ɗan talaka ya auri ƴar masu kuɗi, kuɗin ma irin na gidan Alhaji Sufi Ado Garko da Alhaji Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. Lallai wannan abun ayi koyine gaskiya dan sun kafa tarihi matuƙa. Washe gari asabar biki ya koma gidan su Amarya Mawaddatan’warahmah Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. ALLAH sarki Uncle Yousuf, yau dai kam duk sai jikinsa kuma yay sanyi, dan haka tun da safe yasa aka kira masa Mawaddat ya lallasheta sosai da mata nasihar ta nutsu dan ALLAH ayi komai yanda wani bazai fahimci akwai wata a ƙasa ba. Ayi a gama cikin farin ciki. Yanda taga yanata lallaɓata da nuna damuwarsa sosai, ga dangin mahaifiyarta tako ina kowa na tattalinta da janta a jiki musamman auntyn ta matar Uncle Khamil Aunty Naja’atu ta Abuja da tasu tazo ɗaya daman. Ga ƴan uwanta su Amrah nane da ita, su twins kansu yau har murmushi sukai mata da tsokanarta da amarya suna faɗa mata har sun fara kewarta duk sai ta karaya harda kukanta. Gefe kuma rashin samun kayan shaye-shayen ta na samunta, ya kumayi matuƙar tasirin sake sanyaya mata yanayi yau ba masifa ba ko maganar kirki ma bata iyayi. Ga mafarkin mamarta da tayi a daren jiya shima ya tsaya mata a rai. Duk sai komai ya haɗu ya tankwarata a yanda su Uncle Yousuf basuyi zato ba. Mai kwalliya ta musamman aunty Naja’atu tazo mata tun daga Abuja, kuma daga Lagos ma aka ɗakkota. Ga Mommy ta mata akwati guda na kayan fitar biki masu tsadar gaske. Dai-dai da gold Mawaddat an saya mata na nunama tsara ne, karku manta itace za’a fara aurarwa a jiƙamshi family bayan auren Daddy da na Uncle Yousuf…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣4️⃣
…….Itace ɗiya ta farko da zasu aurar. Dan haka kowa burinsa nuna mata ita ɗin cikakkiyar ƴar gata ce. Hatta Hassan da Hussaini ba’a barsu a baya ba wajen nuna tasu bajintar ta saya mata ƙyauta ta musamman. Ƙyau iya ƙyau Lulu ƙamshi tayisa. Dan a yau ta fito a ƙamshinta babu ƙarya. Da safe sunyi kamu anan cikin gidan Uncle Yousuf kamar yanda ƴammatan family ɗin Garko suka shirya, kamu ne da sisters event a tare, abin ya ƙayatar sosai. Yayinda Lulu ta zama ƴar kallo kawai tana mamakin kanta matuƙa wai a matsayin matar Aliyu driver ɗinta fa, wannan illiterate ɗin nan velleger da take faɗi kullum. (Ki kwantar da hankalinki auren wata ɗaya ne fa kacal, yanzu ma anci sati ɗaya a ciki, duk wannan taron da kike gani nuna komai ba komai ba ayishi shine mafitar da wani bazai zargi komai ba balle Baba ya ce zai aura miki ɗaya da ga cikin su Hon. Haruna) waɗan nan kalaman na Uncle Yousuf ne ke ƙara mata ƙwarin gwiwa da nutsuwar shanye komai ta na bin kowa da ɗan murmushin yaƙe. Sai yanda ƴan uwanta keta haba-haba da ita musamman yayunta maza biyu da sai zuwa suke ɗaukar hoto da ita na ƙara sakata jin daɗi. Mubeen da su Afrah kam ai sune ma kamar ƙawayen nata. Ko’ina suna nane da ita, duk sherin da akema Mubeen na kasancewarsa namiji bai bar wajen ba. (Wannan duk yana cikin shirin Uncle Yousuf daya tattarasu bayan ya tsigesu da masifa ya koma lallashi da nasiha tare da tsara musu yanda zasu kasance da ita a wajen taron bikin dan su taimakawa nutsuwarta komai ya tafi dai-dai. Sun kuma yi ɗin suma har a cikin ransu suna jin daɗin hakan kuma). Bayan tashi da ga kamu & sisters event aka ɗunguma da amarya zuwa gidan Daddy inda Mommy da Aunty Saliha zasuyi yinin biki. Gida ya cika tanƙam d jama’a, kowa burinsa yaga amarya data sake shiga ta musamman acikin wani ubansun shadda da taci aiki mai ƙayatarwa. A take ƴan uwa da abokan arziƙi suka zagayeta ana kwarara mata addu’a, sai ga Lulu da hawaye dan gaba ɗaya jitai komai ya sake kwance mata. Balle ma da Daddy ya rungumeta shima yana hawayen. Hotuna dai an shasu kala da iri har babu adadi. A sannan ne kuma tawagar dangin ango su Aunty Bilkisu da basu sami zuwa Kamu & sisters event ba suka isa gidan. Karan farko da sukaga amaryarsu, itama ta gansu. Duk da ba ƴan ɗakinsu kawai bane a kallo ɗaya Lulu ta gano tsananin kammanin Smart a fuskar Hawwah da Aunty Bilkisu. Yanda kuma suka nuna kulawarsu gareta da yanda Hawwah keta faman kiranta da auntynsu duk da tasan ta girme mata ya sata jin wani irin kimarsu da kwarjini. Suko sun ruɗe matuƙa dajin daɗin ganin yanda Yayan nasu ya samo tsuƙeƙiyar mata ƴar gata kuma ƴar ƙwalisa. Da zasu wuce tasa su Amrah ƙara musu gift da aka raba duk da an basu. Hakan da tayi sai ya ƙara mata kima a idon su Aunty Bilkisu suka tafi suna mai yaba mata da murnar kasancewar ta tasu. Duk da ma kwalliyar fuskarta yasa basu gano cewar itace lawyer ɗin nan dake matuƙar burge Ammah ɗinsu ba. Koda suka isa gida camma dai yau cike yake, dan ma sai gobe in ALLAH ya kaimu Ammah ke yinin bikinta, amma hakan bai hanasu kutsawa su kai mata abinda aka basu a gidan su Lulu ba da yabama tarbar da akai musu da karramawar da amaryar ta sake musu. Hakan bai ishi Hawwah ba sai da ta kira Smart da ke tare da su Ahmad acan stadium ana shirin buga gagarumin ƙwallon da coach ya shirya ta kwankwasa masa labari. Ta kumace ya buɗe data ta tura masa hotunan amaryarsa. Shi da farko baima yarda wai Lulun ce tai musu abinda ta faɗa ɗin ba, dan shi dai yasan wacece ya aura basai an bashi labari ba. Dan haka koda ya yanke kiran ma bai buɗe data ɗin ba ya cigaba da harkokin gabansa. Shi dai Coach ya hanashi shiga wasan, dan haka yana cikin ƴan kallo kawai. Stadium ɗin tayi matuƙar cika maiban mamaki, can dai kamar wanda aka tsikara ya ciro wayarsa da ga aljihu ya buɗe data bayan ya shiga WhatsApp nashi. Akan idonsa hotunan suka buɗe zuciyarsa sai motsi take a ƙirjinsa, sai yayi kamar zai fasa sai kuma dai ya daure har suka kammala buɗewar dan sunada yawa. Hoton farko dai babu ita a ciki, na biyu ma haka. Na uku ita kaɗaice zaune ta kare fuskarta da waya alamar bata son hoton, yawu ya haɗiye a hankali dan duk da fuskarta bai fito ba tayi ƙyau. Ƙara matsawa yay na gaba ananne da sai da tsigar jikin yan maza ta tashi, ya ɗan lumshe idanu ya sake buɗewa yana mai furzar da huci kaɗan. Anan kam raɗam ta fito daga sama har ƙasa aka ɗauketa kuma, ta ɗan juya Luluu eyes ɗinta gefe kaɗan tana kallon gefenta. Ɗan bakin masifar nan da yaci lipstick pitch da maroon kaɗan yay wani irin masifar fidda shape ɗin sa. Haka ma zagayayyar fuskarta mai ɗauke da hanci da yay dai-dai da ita ga manyan idanu masha ALLAH. Yau ne karo na farko da ya ga kwalliya a fuskarta. Sake furzar da iska yay kaɗan gaba ɗaya ma ya rasa yazai fassara yanayin da ya shiga. Sai kawai ya zaɓi kife wayar ya ajiye yana mai harɗe hannayensa a ƙirji ya kwantar da bayansa zuwa kansa luf a kujerar da yake zaune ya ɗan lumshe idanunsa sai dai bai rufesu duka ba yana kallon tarin abokan kwallonsa da sukazo da ga gari-gari domin tayashi murnar aure ƙasa-ƙasa.
Suma wasan nasu yayi ƙyau, sai da akai kiran magrib suka tashi sai kuma an haɗu a wajen dinner, dan Coach shi yay ƙoƙarin bama baƙinsu masauki duk da wasu ma sai yau suka iso dai shine kuma mai gayyatar da Ahmad. “Wai ya naga duk jikinka yay wani laƙwasa ne? Ko ciwon kanne bai saukaba still?”.
Cewar Ahmad cikin damuwa. A hankali ya ɗan furzar da iska tare da shafo goshin nasa ya ce, “Ai ciwon kan nan inaga kozai barni sai an gama hayaniyar nan. Harma na saba da shi a kwana biyun nan”.
Sannu Ahmad ɗin yay masa cikin damuwa. A haka suka ƙarasa gidansu Ahmad ɗin dan acan zasu yi shirin tafiya dinner ɗin, kafin su wuce su ɗauki amarya a gidansu…..
*_DINNER HALL_*
Ƙaton waje ne na gaske Alhaji Sufi Ado Garko ya kama domin ya gayyaci manyan abokan kasuwancin sa dana siyasa a ciki da bai ɗin Nigeria. Gashi kuma mafi yawansu sun san Daddy shima tun da babban yaronsa ne na amana da duk wanda yasan Alhaji Sufi Ado Garko to yasan wanene Alhaji Isma’il Ibrahim Jiƙamshi a wajensa. Iya tsaruwa wajefa ya tsaru, ga abinci iri-iri an tanada. Haka ma manyan mawaƙa na Hausa dana turanci duk sun hallaro. MC kansa mashahuri aka ɗakko domin gabatar da komai. Ta gefe ɗaya ƴammata da samarin Garko family da suka haɗe da jiƙamshi family sun haɗa babban show mai ƙayatarwa domin nishaɗantar da jama’a. Duk da girman wajen da alamu ya nuna zai ɗauki mutane masu yawa duk wanda zai shiga sai da i.v ɗin sa ne zai zama masa gate pass. Dan haka su kansu su Smart da ahalinsa suka shirya komai a tsari domin mutunta kansu a wajen. Duk da dai Alhmdllh ALLAH ya riga ya mutuntasu, tunda da har zuwa yanzu babu wata ɓaraka data shiga na raina juna a tsakani, ko Umma daketa neman hanyar baƙanta Smart wajen wani a cikin dangin matar tasa har yanzu ALLAH bai bata damar ba. Kafin takwas waje da ya cika yay hani’an da manyan mutane ƴan siyasa da ƴan kasuwa har ma da ƴan bokon da iyalansu. Kowa ka gani shar da shi, dan duk da ba’ai anko da zai zama komai da komai iri ɗaya ba sun rubuta kalar kayan da ake buƙatar ƴammata da samari duk su saka. Koma wani iri ne ka saka kala kawai ake buƙatar tazo ɗaya. Manya ne dai kowai yay yanda yake so….
Masha ALLAH na faɗa a lokacin da idanuna suka sauka akan ANGON ƙamshi Aliyu Hydar Smart mai masoya da yawa cikin wata dakakkiyar shadda mai tsananin ƙyau da maiƙo taji aiki na musamman. Itace kawai abinda ya yarda ya amsa da ga dangin amaryar tasa dan Baba ya aiko masa da ita matsayin wadda zai saka a yau ɗin, kamar yanda itama amarya ganin nata kawai tayi. Farar shadda ce da akaima wani shegen ƙawataccen aiki da kalar golden mai ɗaukar ido. Takalmar ƙafarsa haif cover suma golden da ratsin fari, haka ma hularsa golden da ratsin fari kaɗan. Sai agogonsa golden shima. Ga gyaran fuska da ya ƙara masa kwarjini da cikar kamala an masa. Sam wannan Smart ɗin ya banbanta da wancan Smart dirver da kuka sani. Ƙamshi har ba’a magana. Tun a gida Ahmad ke jera mar hotuna dan yakai a ɗaukesan. Ya kuma tubure bazai tafi ba sai yaje Ammah da Abba sun gansa. Dole sai da su Ahmad suka kaisa gidan kuwa Ammah da Abban suka gansa da tsaffin da bazasuje dinner ɗin ba. An masa hoto da iyayensa Abba ya rungumesa. Duk kauce-kaucen Ammah sanda za ɗauke su hoto itama sai ya kwanta da kansa a kafaɗarta, hakan yasa ta juyo kamar zata hararesa shi kuma yay murmushi cikin salon shagwaɓe fuska, ga Abba ya kallesu shima yana murmushi. Hoton sai ya zama na musamman……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣5️⃣
……Daga nan gidan Daddy suka ɗunguma ɗaukar amaryar ƙamshi. Lulu lu’u-lu’un Jiƙamshi family, tauraruwa abar buƙatar son ganin kowa.
“Ya arrahaman!” Ango Smart ya ambata a hankali lokacin da Hussaini ke fitowa da ga gidan riƙe da hannun Lulu. Ni kaina masu karatu sai da alƙalamina yay adungure ƙasa da ƙyar na kamosa na cigaba da muku burutun. Amarya da tayi jiƙaƙƙen ƙyau, idan nace muku ƙyau ina nufin ƙyau maƙurar ƙurewa a cikin ƙarshen ƙure. Wani irin shegen material ne golden color da aka ƙawata da adon fararen stones masu walwali da ɗaukar idanu. An masa ɗinkin gown data kama mata jiki, sai aka ɗaura wani ƙawataccen alƙyabba fara da adon golden kuma a sama, ta rufe jikinta gaba ɗaya tana ɗan jan ƙasa kaɗan. Ɗauri iya ɗauri, ga shi kwalliyar da akai mata ƴar dai-dai misali da bata ɓatar da ainahinta ba a yanzu. Kayan yari komai yaji, ƙamshi kam ba’a magana wayyoni ALLAH kai jama’a. Yaufa Lulu ƙamshi a ƙamshin take ɗan gaske. Takalman ƙafarta su kansu abin kallo ne, suma farare ne da kwalliyar golden sai pos ɗin ta itama farace da kwalliyar golden stones. Kamar shock ne ya jasu a lokacin da Hussain ya kamo hannun Smart ya saka masa na Lulu. A tare suka zabura zasu janye amma tsabar muguntar Hussain ya sake riƙewa gam ya hana hakan. Duk sai sukai diri-diri da idanu (kamar an kama suruki a ɗakin ƙawar kakar matarsa😂😜) cikin wani irin malalacin yanayi ta sakar ma Smart kasalalliyar Harara. Sai kawai ya samu kansa da ramawa shima. Shi Hussain ma sai abin ya bashi dariya. Amma sai ya danne daƙyar baiyi ba ya sake matse hannayensu cikin na juna da faɗin, “Yayana Aliyu Hydar Zakin zaki ga amanar ƙanwata na baka, har abada bana son ka saki wannan hannun ya kasance cikin laluben naka dan ALLAH”.
Smart da Adams apple ɗinsa keta kaikawo a maƙoshi ya saki murmushi mai sanyi da faɗin, “In sha ALLAHU Yaya Hussain. Na kuma gode”. Murmushin jin daɗi Hussain ya saki jin Smart ya kirashi da Yaya, duk da kuwa yasan Smart ɗin zai iya girmarsa da kusan shekaru biyar ma. Hannayen nasu ya saki yana kallon fuskar Lulu da tai wani irin yin takwaf-takwaf tana neman zame hanunta dake cikin na Smart shi kuma ya hana faruwar hakan ta hanyar damƙesa da kyau, kansa ya girgiza mata da ɗan lumshe idanu alamar lallashi irin na yaya da ƙanwa. Dole ta haɗiye abubuwan da ke mata kaikawo a zuciya da maƙoshi a tare, Hussain ya buɗe musu motar da Ahmad ke ciki yana jiransu a mazaunin driver. Ita ta fara shiga, sannan shima Smart ɗin ya shiga, sai kawai Hussain ya shiga gaba dan Uncle Yousuf ne duk ya tsara musu hakan saboda dai kar mutuniyar ta bada ƙafa🤣 dan tabbas zata iya maida hall ɗin kudanci da ga gabashin da yake a gine😂. Ganin Hussain ɗin kam ya sake saka mata nutsuwa da ƙwarin gwiwa harda sauke ajiyar zuciya kamar Smart ɗin yazo ɗauketa kenan😂. Bata ƙara yarda ta kallesa ba duk da harga ALLAH ya matuƙar canja mata tamkar bashi ba. Ta kuma saka pos ɗin ta a tsakkiyarsu alamar karma yace zai raɓeta. Shima dai dama baiyi niyyar hakan ba, shiyyasa yay zamansa sosai jikin ƙofa suka bada gaf sosai a tsakkiyar. Da ga Ahmad har Hussain sai da suka ji dariya a zukatansu saboda yanayin zaman amarya da angon. Ga shi kowa ya juya kai ya kalli waje tsabar babu ruwan wani da wani ma kenan. Sai da suka fara tafiya Hussain da Ahmad suka gaisa. Da ga haka sukacigaba da ƴar hirarsu a hankali su biyu har suka iso. Wajen fita ne fa dole dai Lulu ta haƙura Smart ya fara fita, dan shine ya buɗe mata da kansa ya kuma miƙa mata hannunsa alamar ta ɗora nata. Ƙaramar Harara tai masa tana ɗauke kanta, sai kawai ya cije lips ɗinsa tare da ranƙwafowa gaba ɗayansa yana tattare hannun rigarsa bayan ya cire link ɗin, miƙa hannun yay alamar zai ɗauketa. Da wani irin bala’in sauri ta waro duka manyan idanunta waje da faɗin, “Kuttt! Mi zakayi?!”.
“Ɗaukarki mana. Ba haka kike buƙata ba Madam”. Ya faɗa cikin salon ɗage gira ɗaya da kashe ɗayan idon. Tsabar abinda ya tokare maƙoshin Lulu sai taji kamar ta buɗe dukan muryarta ta ƙwala ihun da kowa da ke hall ɗin sai ya fito ma. Ta tsani wannan Madam ɗin da yake kiranta da shi tun daga randa sukaje duba shi. Ganin yanda ta fara cika ya sashi ɗage duka hannayensa (alamar wanda yay surrender) da gyara ranƙwafar da yay yana dungure kansa da faɗin, “Kai Aliyun nan ka nutsu a gaban Madam kake”. Sai kawai ta ƙara watso masa harara da tura baki gaba. Da sauri ya ɗauke idanunsa dan harga ALLAH sai da ƙassan jikinsa suka amsa akan tura bakin nan. Hussain dake dariyar drama ɗin tasu ne ya katsesu da faɗin, “Sorry kinjin Sister bashi hannun kinga su Baba duk suna ciki shigowarku ake jira kawai a fara abinda ya tara mutane”. A hankali ta ɗago yatsunta uku batare data kallesa ba. Shima sai ya saka nasa ukun tsakkiya kamar yanda tayin yana ɗan taɓe baki kamar yanda tayi, sai da ya riƙo hanun nata baki ɗaya sannan ya rumtse cikin nashi. Koda ta fito bai yarda sun bar jikin motar ba sai da yasa ɗayan hannunsa da kansa ya gyagygyara mata rigar alƙyabbar da ƙyau yanda ta sake suturta kuma hakan bai hana fitar ƙyaun da tai ɗin ba. Da ga haka suka ƙarasa inda abokan ango dana amarya ke jira suka tafi a nutse kamar yanda ake raka amarya da ango ƴan gata zuwa ga hi table. Matuƙar birgewa sun burge mutane da yawa, yaro da babba ƴammata da samari. Taro ne da ya haɗa harda manyan mutane da iyaye da kakanni shiyyasa babu wata shiririta ko baɗala a cikinsa. Amarya da ango ma tunda aka kaisu mazauninsu hatta cake a zaunen suka yanka shi. Koda ta ɗibo danta bashi maimakon yin hakan saita lakata masa a hanci. Abin ya burge mutane da basu dariya, dan yanda tayi ɗin sai ka ɗauka duk cikin soyayya ne, itako tayi hakanne danta bashi haushi.
Shima daya ɗibo ya kai mata baki, buɗewa tai tana shiryama ranta muguntar gallara masa cizo a yatsun dake riƙe da cake ɗin, amma sai da yaje gab da bakin nata sai ya juya hannun ya lunƙuma a nashi bakin yana mata gwalo. Ai hall ɗin kamar zai fashe dan dariya saboda yanda ta sakankance zatayi mugunta amma aka rusa mata plan. Pos ɗin hannunta ta ɗan buga masa a damtsen hannu tana hararasa kamar zatayi kuka dan haushi.
“Aliyu abin tausayi wannan harara dai ka banu da ita kai kam. Anya an taɓa angon da yasha harara a ranar aurensa sama da ni?” ya faɗa yana mangare kansa da kansa. Karan farko ya bata dariya amma sai ta gimtse, tama ɗauke kanta gefe tana ɗan taɓe baki, dan yau sam bata da ƙarfin yin masifa kuma. Da ƙyar aka samu hall ɗin ya lafa da dariyar batun cake aka cigaba da abinda ya tara mutane. Ko sau ɗaya Smart bai yarda ya tashi ba hakama Lulu bai bari ta tashi ba. Da an buƙaci ganinta a wajen fili zai riƙe mata hannu ya girgiza kansa, itama ɗin dama bata da sha’awar tashin, saita fisge hanunta tana harararsa dan yau ita kaɗai aketa faman antaya masa buhu-buhu. Har fa dai MC ya fahimci ango bai san amaryarsa ta tashi kamar yanda shima bai tashi ba. Masu musu liƙi ma dai sai dai su samesu anan. Alhamdullah duk wanda ya shigo wajen nan zai tabbatar maka yaci ya ƙoshi har ma da ƙullar takeaway, Smart ya gaisa da mutanen da bai taɓa tunanin ganinsu koda a zahirin rayuwa ba, dan ƴan siyasa sun halarci taron nan matuƙa da manyan ƴan kasuwa. Har akai aka tashi bayan cake ɗin nan da ruwa baici komai ba a wajen, hakama Lulu ita daman cikin nata ya riga ya naɗe abincin ba damunta yay sosai ba. Ganin dare yayi dan sha biyu ta gota sanda aka tashi Uncle Yousuf yace su Smart ɗin suje gida abinsu zai koma da Lulu gida, dan tun a hall ɗin ya ga Smart nata faman dafe kai alamar bayajin daɗi dauriya kawai yake yi. Yako ji daɗin hakan da Uncle Yousuf ɗin yay musu, itama kuma mai gayya mai aikin taji daɗin hakan, dan ko sallama bata tsaya sunyi ba tai gaba tai shigewarta mota tana zare alƙyabba ɗin tata datai mugun damunta ita da ɗaurin ɗan kwalin….
*_WASHE GARI_*
Washe gari safiyar Lahadi aka tashi da shirin kai amarya Lulu. Dan haka da safe Uncle Yousuf ya ɗauketa da kansa ya kaita gidan Baba. Inda yayye da ƙannen mahaifiyarta suka taru domin mata nasiha. Alh. Sulaiman ne kawai babu, sosai zuciyar Lulu tai matuƙar rauni, dan mahaifiyarta ce kawai babu a wajen bayan mahaifin Tajuddeen. Ita kaɗai suka taɓa rasawa a cikinsu……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣6️⃣
……..Kuka ne sosai ya kufce mata, dan matuƙa tana so da begen mahaifiyarta. (Dan Lulu ta kasance irin yaran nan ne masu ƙulafucin uwa, sai kuma gashi ALLAH bai ƙaddara zata rayu da ita ba) kukan nata ya sake karya zuciyar iyayen nata, haka ma Baba duk da dauriyarsa sai da yaji ƙwalla sun cika masa ido. Hannunta ya kama ya zaunar a kusa da shi tare da ɗora kanta a kafaɗarsa ta dama yana ɗan bubbuga bayanta alamar lallashi. Sai da suka samu taɗan tsagaita kukan sai ajiyar zuciya da take faman saki sannan baba ya fara mata nasiha. Bayan ya gama kowa a falon yay tasa. Kakarta da suke kira Dada ma dai ta danne abinda ke ƙasan ranta na ƙiyayyar auren tai mata nasiha sama-sama, dan ta ɗauki alwashin sai inda ƙarfinta ya ƙare wajen raba wannan auren ƙaddarar. Komai da suke faɗa yana shiga kunnen Lulu, sai dai zuciyarta na fassara komai da gargajiyanci da kuma tsauri da yawa saboda ita tunaninta daban da nasu kasancewar babu ilimin addini a tare da ita. Kuka ma da sukaga tanayi na tuna mahaifiyarta ne kawai babu na aure dan a wawtarta auren nan dai na wata ɗaya ne kacal. Duk wata ƙyauta da iyayen nata suka shirya bata anan wajen suka bata ita kamar yanda tsarin family ɗin yake. Bayan an gama Uncle Khamil da Uncle Shu’aib suka ɗauke ta suka maida gidan Daddy dan Uncle Yousuf yana ajiyeta ya juya. Acan ɗin ma dai bayan sallar azhar Daddy da Uncle Yousuf, Mommy aunty Saliha da gayyar iyaye ƴan jiƙamshi suka zagayeta da tasu nasihar, duk da dai Daddy baice komai ba, sakamakon gaba ɗaya yanayinsa ya sauya, jikinsa duk a sanyaye yake alamar damuwar rabuwa da ƴar tashi. Sai dai yana ƙoƙarin dannewa amma hakan ya gagara. Bayan tashi da ga wannan zaman aka cigaba da kimtse-kimtsen tafiya da amarya, yayinda Aunty Saliha ta sake ɗaukar Lulu ta kaima matan nan masu gyarata suka sake murjeta tas da kayan gyaransu na musamman da tarin ƙamshi kala-kala. Ba kuma a maidata gidan Daddy ba sai huɗu na yamma cikin shirin miƙata gidan iyayen mijinta. Tayi ƙyau matuƙa cikin atamfar da Aunty Saliha ta bata ta saka. Aka kuma ɗora mata alƙyabba ƴar ubansu baƙa mai kwalliyar golden da fari kaɗan, sai stones da suka sake ƙawatata. Shara-shara alƙyabbar take. Takalmanta yau ma flat ne baƙaƙe. Babu kwalliya ko ɗis a fuskarta dan tace bata so. Sai dai hakan bai hanata zama mai cika ido da kwarjini irin na amare ba, ga gyara tasha na fitar hankali dama fatar nan ta sake wani irin ƙyau kamar madara a sabuwar ƙwarya (Dangin Smart ban son jealous 🥱😉) Hankalin Lulu bai tashi ba sai da taga Daddy na hawaye sanda aka fito da ita yana riƙe da hannunta zai sakata a motar da Hassan zai ja, dan sune zasu mata rakkiya shi da Hussain da Mubeen. Sai motar ƴan rakkiyar amaryar su biyosu a baya. Duk da abokan ango sunzo kasancewar amaryar ƴar dangi ce akwai zugar motoci da ga family ɗin biyu na Jiƙamshi da Garko da zasu bisu da nasu motocin. Ba Daddy kawai ba Uncle Yousuf kansa yana can falon Daddyn yana sharce hawaye yamaƙi fitowa shi. Lulu da duk taji karaya tamkar ba ita ɗin nan ba ta rungume Daddy ta saki kuka mai ban tausayi. Itafa auren nan baisa taji komai, amma wasu abubuwa da ga zuri’ar tata kansa zuciyarta ta motsu. Da ƙyar Uncle Khamil ya janye Lulu a jikin Daddy aka sanyata a mota, Hussain da Mubeen suka sata a tsakkiya, gaba kuma Amrah da Afrah ne sai Hassan da zaija motar.
Masha ALLAH motocin rakkiyar Lulu sun ratsa kwaryar Kano ne tamkar wata gwamna zata gitta dan gatan da zuri’arta suka nuna mata. Duk inda suka ratsa sai anso jin wanene haka? Koda babu mai bada amsa. A haka suka iso anguwar fagge layin su Smart. Yanda aka jera motocin tun daga ƙofar gidansu har kusan ƙarshen titin ya sake ɗaukar hankali matuƙa, hatta mata dake cikin gidaje fitowa suke leƙen wannan sabon lamari, lallai an sake shaida Smart kam dai ya ɗakko ƴar gidan madara.
Smart da ƴan uwansa mazan gidansu suna falon Abba daya tarasu su duka amaryar ta iso. Daga ɗakin suna iya jin surutai da gidan ya ɗauka da kambama yawan motocin da suka rako amarya. Balle ma motar da aka kawota ciki ta musamman ce da Daddy ya saya mata matsayin gift na aure. Tasha adon ribbon kuwa da balun masha ALLAH. A hankali Smart da ke kusa da Rufa’i mai bi masa babban ɗan Mama ya lumshe idanunsa yana jin wani irin yanayi mai wahalar fassara na saukar masa. Addu’a ya shiga karantowa game da wannan aure nasa mai cike da rikici takowane ɓangare. Ita kanta amaryar da nata.. Addu’ar Smart kamar an saita dai-dai da fitowar Lulu amaryar ƙamshi da ga mota Mubeen riƙe da hannunta. Fuskarta rufe take ruff da hular alƙyabbar dan haka ba’a iya ganinta tako ina sai hannunta mai ƙawace da adon zanen lalle ja da baƙi. Da wani sirrintaccen ƙamshi na musamman mai ratsa ɓargo da jijiya. Har cikin gida Hassan da Hussain da Mubeen da su Afrah sukai mata rakkiya, hakan ya matuƙar sake burge mutane da kallon al’amarin matsayin shaƙuwa ce ta kawo hakan tsakaninsu. Sun kaita har ƙofar falon Ammah da ke cike da ƴan uwanta itama, da ga nan Aunty Saliha da Aunty Naja’atu suka kama hannunta suka ƙarasa da ita cikin falon Ammah. Da ga haka su Hussain suka juya cikin sanyin jiki da basu taɓa tunanin zasu iya ji akan Mawaddat da sukai ƙololuwar tsana a cikinsu ba dalilin fifitata da mahaifinsu yay sama da su da mahaifiyarsu. Mubeen ma sai kawai ya kama hawaye….
Sauran ƴan rakkiyar amarya sun ɗura ciki suma. Wasu farin ciki ya kawosu wasu ko gulma da jinjina inda ALLAH ya kawo Lulun. Duk irin yanga da jin kai da izza irin tata ta ƙare da aure a getto eria irin haka? Kai lallai da mamaki koda yake tarihine ya maimaita kansa tunda haka itama mahaifiyarta tayi, sai dai akwai banbanci sosai a yanayin tsarin auren. Wasu ma harda dariyar mugunta wasu ko tausayinta suke ji a nasu ganin taci baya gaskiya. Wasu ko tayata farin ciki suke ALLAH ya kawota matakin da ko wacce ɗiya mace ke jin alfahari da ɗaukaka. Abu mafi ɗaukar hankali tarbar mutuntawa da suka samu daga ahalin ango duk da yawansu. Ammah kam da ga ciki su Aunty Nasara na shiga da Lulu ta taso ta rungumeta a jikinta. Haka ma ƴan uwanta sai faman musu lale marhabun akeyi. Ajiyar zuciya Lulu ta dinga saki da sake lafewa aikin Ammah, dan wata irin nutsuwa taji tana ratsa mata sassan jiki da ɓargo batare data san dalili ba. Duk da bata san wacece ita ba, ba kuma ta gani fuskarta abinda matar tai mata ya sata jin ƙaunarta. Bayan kakarta Dada Ammah ce mace ta biyu datai mata runguma irin ta mahaifiya, a hankali hawaye suka shiga ziraro mata daga cikin hular alƙyabbar tsigar jikinta na wani irin tashi. Adda Fati babbar yayar su Ammah da suke uba ɗaya ce tazo ta kama hannun Lulu aka shiga da ita ƙuryar ɗakin Ammah da aka gyara dama dan tarbar amaryar, shiyyasa kowa ya fito aka dawo falo da ɗayan ɗakin dan kowance a gidan dama ɗakuna uku ne a falonta.
Gida ya sake amsar harami tako ina, dan ƴan kawo Lulu basu wuce ba sai kusan biyar da rabi na yamma. Lulu na can ƙuryar ɗakin Ammah tare da su Amrah dan ita dai fa babu ƙawa, dama da lafiya-lafiya ne da Nadiya ce zata kasance da ita. Sai dai ta riga ta jingine tarayyarsu a matsayin tarihi ita kuma idan ta ɗana tarkon tafiya bata waiwaye. An tara musu abinci da abin sha kala-kala har da su fura mai ƙyau da tsafta. Aiki su Amrah suka shiga cin nama da furar nan dan sun musu da ɗi. Da farko dai Afrah zata fara wani iyayi Amrah tai mata gargaɗi da tuna mata kashedin da Mommy tai musu. Hakan yasa ta dawo hankalinta, sai da suka buɗe abincin kuma taji ɗanɗano sai ta ware ta hau ci. Duk abinda suke Lulu na kwance lamo a gadon Ammah tana kallonsu kawai. Kanta ke mata wani irin masifar ciwo, dan tana cikin matsanancin buƙatar kayan shaye-shayen ta matuƙa. Kwana bakwai fa kenan bata sha komai ba, kai ai tayi ƙoƙari matuƙa. Har ji take ana mata mutsu-mutsu a brain, ga hayaniyar bikin nan na matuƙar caja mata kai itama. Dan ma nan ɗin da aka kawosu su kaɗai ya mata daɗi, duk da sunajin hayaniyar amma da sauƙi ba kamar suna a wajen ba. Su Aunty Saliha basu wuce ba sai bayan magriba su, ƙin shigowa sukai mata sallama dan karsu takalo ta, bayan wucewarsu ma cikin gidan ta fara lafawa da mutane, dan dj da su Mubarak suka sa ya kwashi mata duk anyi waje. Tuni su Amrah ma da ke jiyo sautin kiɗa suka gudu suka barta ita kaɗai a ɗakin. Batace musu komai ba sai lumshe idanunta da tai barci ya kwasheta, cikin mintina ƙalilan zazzaɓi mai zafi ya rufeta ruf ta hau rawar sanyi, ga fanka na juyawa a ɗakin ta kasa tashi ta kashe ta. Barcin take a wahale ga mafarkin mahaifiyarta……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣7️⃣
……..Wajen ƙarfe tara ALLAH ya kawo aunty Bilkisu ɗakin zata ɗauki kayan biki data ɓoye dan bama facalolinta da zasu wuce. Da sauri ta ƙarasa gaban gadon tana ambaton sunan ALLAH. Ta kai hannunta a goshin Lulu dake barci. Zafi zau har tana jin harbawar jijiyoyin kan nata. Bargo taja ta lulluɓa mata, sannan ta kwashi abinda tazo ɗaukar ta fice. Bata san yin kwakwazo hankalin mutane ya dawo nan, dan haka ta sallami facalolin nata sannan ta koma cikin raɗa ta sanarma Ammah da ke a cikin danginta da zasu kwana. Hankalin Ammah ma ya tashi, ta miƙe cikin hikima ta shiga bedroom ɗin, itama dai tattaɓa goshin nata tai, sai kuma ta juyo tana kallon Aunty Bilkisu.
“Yanzu ya za’ayi kenan? Dan nima bana son kowa ya fahimta baki baka san yanda na wani yake ba”.
“Hakane Ammah, to kodai a kira Hydar, sai ya samo mata magani”.
Ɗan jimm Ammah tai na tunani, sai kuma ta ɗan sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Kirashi ɗin to. Ki kuma turomin Auntynku”.
Da to Aunty Bilkisu ta Amsa tana fita, sai da ta fara zuwa tai kiran aunty Amarya da Ammah tace kafin ta wuce sashen samarin gidan. Duk suna waje wajen dj balle ga ƴammata dama cike da gida, dan kusan duk ɗakunan ma a kulle suke, sai ɗakin Smart ne da ya nuna haske ke tabbatar da mutum a ciki. Sallama tayi aka amsa mata sannan ta shiga. Shi da Ahmad ne kawai a ɗakin, dan abokansu su kam yau duk kowa ya kama gabansa tunma da safe kasancewar gobe idan ALLAH ya kaimu Monday kowa zai koma kan aikinsa. Ahmad da ke zaune yana shan fura ya dubi aunty Bilkisu da murmushi yana faɗin, “Aunty Babba ke da kanki”. Murmushin ta mayar masa da faɗin, “To ya na iya Ahmad, amaryarku ce babu lafiya”.
“Ya Salam! Miya faru?”.
Ya faɗa da sauri. Dai-dai nan Smart ya fito da ga toilet da alama wanka yayi, sai dai sanye yake da jallabiya sai ƙaramin towel yana goge sumar kansa. Su biyun duka ya kalla saboda jin abinda Ahmad ya faɗa, da son jin amsar da Aunty Bilkisu zata bada. Cikin damuwa ta ce, “Zazzaɓi ne da ciwon kai mai zafi. Gata can cikin bargo tanata rawar sanyi ma”.
Smart ya ɗan lumshe ido ya buɗe, sai kuma ya ɗauki turare ya ɗan fesa da faɗin, “Inaga hayaniyar nan ce….”
“Hakama Ammah tace, shiyyasa ma tace a kiraka”. Aunty Bilkisu ta katsesa da sauri. Ɗan Basket ɗin da yake ajiye magunguna ya ɗauka, sai kuma ya dubi Ahmad da faɗin, “Ina zuwa”. Kai ya jinjina masa da mata addu’ar samun lafiya. Su kuma suka fice. Cikin gidan da sauƙin mutane dan duk ana waje wajen dj, sai ƴan tsofaffin ne da suka gaji sukai zamansu. Aunty Amarya ce ta taresu tun a farkon shigowa tace su biyota. Binta sukai sashenta, falon babu kowa sai yara da aka kwantar, kuma duk yaranta ne, dan ita danginta ma duk sun wace sai ƙanwarta budurwa da zata kwana tana kuma tare da su Maryam. Kai tsaye bedroom ɗin ta suka shiga, Lulu da aka maido nan tana kwance a gado cikin bargon da Aunty Amarya ta lulluɓa mata. Aunty Bilkisu tace “Yauwa nan aka maidota ashe?”. Amsa Aunty Amarya ta bata da “Eh nan ɗin yafi ƙarancin hayaniyane”. Sai kuma ta kalli Smart da ya zubama gadon idanu kawai batare daya ƙarasa ba. Katseshi tai da faɗin, “Hydar ƙaraso, Bara a samo ruwa tasha magani, sai dai banajin ma tunda aka kawota gidan nan taci wani abu. Ko a ɗan samo mata abinci? Ko tea haka ko”.
A hankali ya ce, “Ko tea ɗin dai zaifi”.
Babu jimawa Aunty Amarya ta dawo da tea da ruwa. Tana ajiyewa suka fice ita da aunty Bilkisu, sai lokacin ya ƙarasa gaban gadon. Da ga tsaye ya kai hannu kan bargon ya ɗan yaye kaɗan idanunsa suka sauka akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta. Kamar ko yaushe yau ma babu kwalliya, sai wani irin sirrintaccen ƙyawu data ƙara fiye da yanda ya santa. A karo na biyu bayan ranar dinner daya riƙe mata hannu ya taɓa jikinta yanzu ma. Saukar hannunsa mai sanyin danshin ruwan wankan daya fito ya sata buɗe idanu kamar a ɗan zabure. Cikin sa’a kuwa suka faɗa cikin nasa saboda shima kallonta yake. Sake waro idanun tai da ƙyau, sai kuma ta kai hannu ta buge masa nasa hannun da har yanzu ke akan goshin nata tana hararar sa. Cikin ƙarfin hali ta ce, “Kai kuma waya gayyatoka nan?”. Yanda tai maganar da son yin masifa sai dai babu ƙarfi yaso bashi dariya, amma sai ya danne abarsa baiyi ba, sai ma kaiwa zaune da yay a bakin gadon har jikinsu na gogar juna sai dai ita a bargo take, kanta ya ɗan kifo yana raba hannayensa gefe-da-gefenta ta kasance a tsakkiya. Idanunta data sake rufewa ta buɗe da sauri jin saukar numfashinsa saman fuskarta duk da akwai ƴar tazara a tsakaninsu, ta sake watsa masa harara ta ce, “Kai kuma wai miye haka? Kake yi”.
Karan farko cikin ɗan lumshe idanunsa da buɗewa a lokaci guda ya motsa lips ɗinsa dan shima dai ciwon kansan nan na tare da shi a yau ma yini guda. Dan ma yanata addu’a da shan addu’oi wajen Malam sannan Abba yay masa kamu ɗazun da magrib shine ma ya ɗan samu barci sai yanzu ya tashi yay ɗan wanka zaiyi sallar isha’i da shafa’i da wutri aunty Bilkisu taje. “Zan dai yi Madam. Amma first ina son sanin mike damunki?”. Yay maganar cikin tausasa harshe sosai.
“Meya ruwanka malam nifa bana son shishshigi ka sani”. Itama ta faɗa cikin tsiwa da takurar yanayin kusancin nasu.
“Inafa na sani, sai dai yanzu da kika faɗa zan kiyaye. Amma yanzu dai ni ba faɗa nazo muyi ba, tashi kici abinci kisha magani”.
“Nace maka ina buƙata ne?”.
“Basai kina buƙata ba ai”. Ya bata amsa yana ɗaura hannunsa saman bargon zai yaye. Tattaro bargon tai ta da sauri ta tattaro cikin hannunta zata fisge daga nashi. Hakan yasa ya ja shima, itama ta ja, ya ƙara ja, itama ta fisga cikin sake fusata duk da bata da wani ƙarfin kirki a jikinta. Ga bakin masifar sai motsi yake alamar magana take son yi amma bata fita. Da ɗan ƙarfi yaja kasancewar ƙyaleta kawai yake dama, aiko ya ɗage bargon. Gaba ɗaya ta tattaro da hannunsa da bargon ta fisgo cikin takaici sai kawai ya biyo su shima ya faɗa mata a jiki fuskokinsu kan na juna kowa na shaƙar numfashin ɗan uwansa, lips ɗinsa a kan nata. Sosai zukatansu suka hau dokawa da sauri-sauri a tare, sai dai kowanne da dalilinsa. Lulu da wani shuɗaɗɗen al’amari mai matuƙar zafafa zuciya da ƙonata ya fara son hasko mata a memory tasa dukan sauran ƙarfinta ta turesa jikinta na rawa. Hakan bai sakashi yin ko gezau ba, sai dai shima ya matsar da fuskarsa da ga kan nata, sai kuma ya ɗagata jininsa na wani yamutsawa. Zaune ta tashi tana ƙoƙarin sauka a gadon kamar wadda ke neman rasa nutsuwarta dan jikinta rawa yake, yay saurin dakatar da ita cikin sassarfar harshe shima. “Ina kuma zaki je?”. Ganin tana cigaba da janye bargon zata saukan ya riƙota da sauri. Harara ta watsa masa da idanunta da suka kaɗa sosai. Ga jikin nata rawa yake da gasken fa. Magana take son yi amma ta kasa, sai idanunta dake cikowa da ƙwalla. Mamaki sosai hakan ya bashi, amma sai ya sake yinƙurin riƙota.
Hannunta ta fisge, sai kuma ta dafe kanta wasu hawaye masu zafi na sake wanke mata fuska. Idanu ya zuba mata ganin yanda jikinta ke ƙara ƙarfin rawa, hakan ya matuƙar sake ɗaure masa kai da zuciya, dan yanayine bawai mai nuna ƙin da take masa ba matsayin wanda bata so ko tafi ƙarfin aurensa, ba kuma kuya bace. Al’amarin nata kamar dai like wadda ta tuna wani mummunan al’amari mai firgitarwa da ciwo a zuciyarta da yay kamanceceniya da yanayin da suke ciki. Kanta ta sake girgizawa da sake yinƙurawa zata ƙarasa sauka ya miƙe da sauri ya zagaya gabanta. Cikin nuna kulawa da son maidota a nutsuwarta ya ce, “Kinga Please relax, ko mima zuciyarki ke son ayyana miki ba haka bane ba, koma ki kwanta kinga baki da lafiya”.
“Idanunta da sukai masifar kaɗawa da ja ta ɗago ta zuba masa. Sai kuma taja da baya da ga kusa da shi har yanzu dai da alamar bata samu nutsuwar da yake buƙatar ba. Shima sai ya matsa ɗin da kallon ƙofa ya kuma sake maido idanunsa kanta. “Kin gane bana son wani ya fahimci akwai wani abu a tsakaninmu saɓanin abinda suke kallo a bayyane. Ki daure zuciyarki na roƙeki koma mi kike tunani ki ajiyeshi gefe”.
Yaraf ta koma saman gadon ta zauna, hannunta dafe da kanta muryarta na fita da rawa da ɗan kaushi ta ce, “Ka kira min wata a cikinsu bazan iya zama da ga ni sai kai a ɗakin nan ba in har dole sai jikinka ya taɓa nawa”.
“Wancan ma mistake ne, bakuma za’a sake ba, Kinga ga tea kisha sai kisha maganin ki kwanta”.
Tabbas yanda yake mata magana a nutse ya taimaka ma ƙwaƙwalwarta wajen dawo da ita hayyacinta kan cewar bafa abinda ke mata kai-kawon bane ba. Sannan kuma tunda take da shi bai taɓa aikata mata makamancin hakan ba, lallai ta yarda mistake ɗinne kamar yanda ya faɗa. Hakane, ƙwarai hakanne mistake ne. Zuciyata ta shiga sake tabbatar mata. Sai ta fara sauke numfashi a hankali a hankali jikinta na ƙara samun ƴar nutsuwa. Gadon ta koma ta zauna ta jingina da fuskar gadon bayan taja bargon ta rufa, sai ya koma shima ya zauna a baki-baki da ƴar tazara a tsakaninsu yana sauke ƙaramar ajiyar zuciya ya miƙa mata kofin shayin da har ya ɗan fara hucewa……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣8️⃣
……..Kai ta girgiza masa alamar bazata sha ba. Sai ya ce mata “Please ko kaɗanne! Kinga magani zaki sha”.
Yanda yay maganar da ɗan dafe kansa shima ya sata amsa dan har yanzu dai tafi buƙatar ya fitan ko zata fi samun daidaito yanda ya kamata. Kwankwaɗar shayin tai kamar ruwa kawai duk da akwai ɗan sauran zafin. Tasha kusan rabi ta miƙa masa kofin, amsa yay baice mata komai ba ganin ta ɗan sha. Ba tsoron magani take ba, dan haka ta amsa tasha shima salin alin, sai kuma ta zame ta kwanta tare da lulluɓe duk jikinta har kanta ta juya masa baya. Idanu kawai ya zubama bargon da take ciki, har yama rasa mizai hasaso game da abinda ya farun yanzu. Rashin makama ya sashi miƙewa da Basket ɗin magungunan, ya ɗan tsaya a kanta yay addu’ar da ake son yima mara lafiya da kuma ta barci ya tofa mata dan yasan idan yace zai tofa mata a hannu ta shafa bazasu wanye lafiya ba. Dan haka yay yanda zata fisheshi sannan ya fice.
Su Aunty Bilkisu na falon zaune da alama dakon fitowarsa suke, bai zauna ba ya ce, “Tasha maganin ta kwanta nima zanje na kwanta sai da safe”.
“ALLAH ya tashe mu lafiya”.
Suka faɗa a tare, yana ida ficewa yake amsawa da Amin. Koda ya koma ɗakin nasa ya samu Ahmad na wanka, dan haka ya zauna jiransa sai da ya fito ya shiga ya sake alwala ya fito. Sallar isha’i ya rama da yin shafa’i da wutri yay karatun Alkur’ani kaɗan dan wancan kiɗan na waje damunsa yake yi. Bai dai ce komai ba yay kwanciyarsa bayan sun ɗanyi magana da Ahmad dake tambayarsa yaya jikin Lulun. Ya amsa masa da cewar da sauƙi zazzaɓi ne. Daga haka ɗakin yay shiru, Ahmad na kallo a MBC Action shi ko yay luf tamkar mai barci, sai dai idanunsa biyu abinda Lulun taine ɗazun ke masa kaikawo a rai. Tabbas akwai abinda ya firgitata a dalilin abinda ya faru a tsakaninsu. Yana kuma tunanin kamar hakan ya tuna mata da wani abu ne da ya shuɗe a rayuwarta ko kuma…. Sai kuma ya ɗan furzar da iska kaɗan, hakanne yasa Ahmad jiyowa ya kallesa.
“Kai wai dama ba barci kake ba?”
Idanunsa ya ɗan buɗe ya kalla Ahmad ɗin. Shi kuma sai ya saki ƴar dariya da faɗin, “Oh dama likimo kayi, to kodai mun tauyeka ne da rashin baka amaryarka? Ai bata ɓaci ba yanzu ma sai a kawo maka ita nan ko kuma ku tashi ku wuce karma ku mana abin kunya an…..”
Bumm!! Yaji saukar filo akan bakinsa. Filon Ahmad ya riƙe yana murza bakin, sai kuma ya kalla Smart dake harararsa ya bushe da dariya. “Kufa dama masu shiru-shirun nan wlhy abin tsoro ne wajen ƙulafucin mace. To maida wuƙar yau ne kawai gobe i war haka kuna can manne…..”
Sake jawo wani filon Smart yay zai jefa masa yay saurin ɗaga hannu sama alamar surrender yana faɗin, “Yi haƙuri nayi shiru Zakin zaki. Haka kawai kamun dogon baki na kasa samun mai aurena nima”.
Ƙwafa Smart yayi ya ajiye filon, sai kawai yaja bargo ya lulluɓa yana juya masa baya ma. Dariya Ahmad ɗin ya cigaba da yi masa ta shaƙiyancin a kaikaice. Shi dai bai sake kulashi ba dan sosai abinda Lulu tai yanzu yay masa tsaye a rai yaƙi wucewa…..
*_WASHE GARI_*
Washe gari safiyar litinin kusan kowa ya tashi da ƙyar musamman ma ƴammatan nan da sukasha rawa da su Abdull da suma suka cashe kam basu tashi ba sai wajen sha ɗaya da ƙyar. Baƙi fa nata haramar tafiya musamman ma na nesa dangin Abba. Dan haka buɗar kai ma da wuri za’ayi. Alhmdllh amarya Lulu ma ta tashi garas babu zazzaɓin, sai dai damuwar son shan kayayyakinta da ke ƙara tsikararta. Tare suka kwana da su Amrah a ɗakin aunty Amarya. Koda aka kammala haɗa break fast Asma’u ce takai musu. Yanda ta gaishe da Lulu cike da girmamawa da kiranta aunty yay matuƙar mata tasiri a zuciya, sai taji ƙaunar Asma’un ya shigeta, gata ƙyaƙyƙyawa, kamanninta kuma sosai a bayyane suke da Smart. Tun jiya sun jone da su Afrah dan zasu iya zama sa’anni, sai dai Asma’u ta fisu nutsuwa a bayyane, su kuma sun fita wayewa. Dan haka ta basu hannu suka gaisa kowanne nama ɗan uwansa murmushi, a take kuma hira ta ɓalle a tsakaninsu sai Lulu ta zama ƴar kallo. Asma’u na tare da su har sai da Amal tazo tai kiranta sannan tai musu sallama da cewar zata dawo idan tayi sallar walha.
“Wannan kuma ina kuka samota?”
Cewar Lulu bayan fitar Asma’u. Kai tsaye Amrah ta bata amsa da “Aunty Lu ƙanwar Uncle Smart ce fa, tace mana itace auta a ɗakinsu. ALLAH yarinyar tana da daɗin zama bakiga yanda suka dinga karramamu jiya ba, mutanen gidan nan nada kirki”.
Shiru kawai Lulu tai tana kallon Amrah ɗin har na wasu sakkani, sai kuma ta ɗauke idanun nata sakamakon kiran wayar Afrah da akayi. Mommy ce, tana ɗagawa tace a Bama Lulu. Amsa tai cike da ɗokin jin Mommy, ta gaisheta da faɗin, “Good morning Mommy”.
Daga can Mommy ta amsa mata da kulawa da kuma tambayarta yanda suka kwana a baƙon guri da bin ba’asin babu dai wata matsala ko?. Samun kanta tai da amsawa Mommy ɗin da “Eh babu wata damuwa Mommy.”
“To Alhmdllh haka akeso. Sai ku zama cikin shiri gasu Auntynku nan tahowa buɗar kai, zasu kuma maidaki gidanki In sha ALLAH”.
Duk da bawani ta damu da zuwa can ɗin ba ko ɗaukar hakan da muhimmanci ta amsawa da Mommy ɗin da to. Da ga haka ta miƙawa su Amrah wayar ta ƙarasa shirinta dan tayi wanka harma ta saka kaya…..
Ƙarfe kusan sha biyu dangin Lulu suka iso gidan su Smart da shatara ta arziƙi na kayan gara dana rabo. Acewarsu waɗan nan iya na nan gidan su Smart ɗin ne nashi kayan garar ankai can gidansu. Koda Abba da aka kira yazo kai tsaye yace musu baza’a amsa ba kayan sunyi yawa. Haƙuri su Aunty Saliha sukaita bashi amma fir yaƙi, ya daice an amshi kayan rabo suyi kamar yanda al’ada ta tanadar amma kayan abinci kam a’a sunyi yawa. Wanda aka kaima Smart ɗin sun wadatar. Dole aka haƙura da sauke kayan daga motar da aka ciko da su sai iya na rabon kawai. Duk abinda ake Lulu taji, hakan kuma ya matuƙar bata mamaki, sai dai batace komai ba. Anyi rabo na bajinta daya tsayama su Umma arai, dan a kaf aurarrakin ƴaƴansu maza ko rabin hakan ba’ayi ba, hatta ƙannen Smart da ke ɗakunansu har ƴaƴan Aunty Amarya sai da aka basu abu, daga haka akai ɗan abinda al’ada ta tanadar ciki harda kai Lulu gaban surukinta Abba da tsirarun ƴan uwansa datai ƙyau cikin lass pitch color da yay matuƙar mata ƙyau skert da riga da mayafinsa, ga kayan sarƙa ta ɗora sai ɗaukar ido take duk da kwalliyar kaɗan ta yarda su Amrah sukai mata. Fuskarta a lulluɓe take, ta gaishesu kamar yanda aunty Saliha ta sanar mata tayi tunkan su fito daga ɗakin aunty Amarya. Abba yay mata tarba irin ta uba da ƴa, ya saka mata albarka sosai da yimata nasiha tare da addu’a, hakama ƴan uwansa. Daga nan ɗakin Ammah aka kaita. Itama dai kamar Abban ne, ta mata nasiha da sanya albarka a wannan aure tare da fatan alkairi. Hakama ƴan uwanta. Sai ɗakin Umma da taso yin abin kunya sai da ƴarta ta kwaɓeta, a hakan ma dai sama-sama tace ALLAH ya sanya alkairi. Hakan bai damu su Aunty Naja’atu ba, dan sun fahimci Umma sai a hankali, mace ce da bata iya ɓoye hassadarta. Sai wajen Mama. Ita dai ta matuƙar dannewa dan ƴaƴanta ita na ƙoƙarin ƙwaɓarta idan sukaga zatayi wata ƙwaɓar, ta tarbesu da yima amarya nasiha a taƙaice itama tai addu’a kuma. Sun koma ɗakin aunty Amarya itama tai fatan alƙawari sosai da addu’a. Sannan aka sake maidata ɗakin Ammah, da ga canne aka ƙarasa abinda ya rage na yima juna godiya da fatan alkairi sannan suka ɗauki Mawaddat domin maidata can gidan da zasu zauna. Baƙi na nan kuma suka ƙarasa shirinsu na tafiya dan jiya duk an kaisu sunga gidan amarya bisa tsarin Abba dan yau kar ta zama sun takura musu.
Sun iso gidan amarya lafiya, Lulu ta buɗe idanu da ƙyau tana kallon ko’ina tunda dai daga ita sai ƴan uwanta. Komai batace ba akan gidan da tsarinsa, ita babbar damuwarta a yanzu kawai ta samu kayan shaye-shayen ta ne, dan shine ya haifar mata da zama shiru-shiru da rashin ƙarfin jiki. Sarai aunty Saliha ta fahimci damuwarta, sai kuma yanzu ta sake gane hikimar Uncle Yousuf da duk ya tsara hanyar toshe mata inda zata iya samun komai da zata sha, dan a dalilin hakan gashi nan sun samu tayi laushin da kowa ke iya controlling ɗinta batare da an samu ko ƙaramar matsala ba. Suna shiga takai kwance a falo ta dunƙule jikinta waje guda ta rufe idanu. Suko suka shiga ɗan gyara abinda zasu gyara su Amrah nata santin yanda gidan ya tsaru duk da bai kasance katafare ba. Sai da suka daidaita komai yanda ya kamata, Aunty Naja’atu ta sakata yin sabon wanka wajen ƙarfe shida na yamma, kafin ta fito sauran mutanen dake gidan duk suka wuce, aka bar su Aunty Saliha kawai sai su Amrah dake ta ƙara goge inda aka ɓata da sassaka turaren wuta. Tsaye sukayi a kanta ta shirya cikin wasu ubansun yadi mai taushi da ɗaukar ido, sai yi take kamar zatayi kuka amma suna lallashinta dan sun fahimci matsalarta, sai dai kowa da yanda ya fahimta ɗin kasancewar aunty Naja’atu bata san Lulu na shaye-shaye ba, dan duk da tamafi samun damar yi idan taje wajensu a Abuja amma iya takunta yasa basu taɓa gane komai ba da ga ita har Uncle Khamil. Sai da suka tabbatar komai ya dai-daita a yanda suke buƙata sannan suka zare jikinsu suka fito a ɗakin, ita dai tana kwance a tunaninta zasuje falo ne, koda taji gidan yayi tsitt barcin dake rinjayar idanunta yasa bata kawo komai a ranta ba ta cigaba da saƙa ta yanda zata samu abinda take muradi……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣9️⃣
……Smart zaune gaban su Abba da Ammah suna masa nasiha. Yayi matuƙar ƙyau cikin yadi mai taushi grey color, ga ƙamshi mai daɗi da saka nutsuwa yana yi. Nasiha mai ratsa jiki Ammah da Abba sukai masa sannan suka rufe da addu’oin samun zaman lafiya da nasarar rayuwa. Tare da tuna masa muhimmancin cigaba da tsayawa akan gaskiya da addu’a da ibada. Kar yaga ya koma bayan idanunsu ya aro halin da basu sanshi da shi ba. Ya ji tsoron ALLAH ya riƙe matarsa da zuciya ɗaya bisa koyarwar MANZON ALLAH (S.A.W) karya barta tai kuka akan abinda yanada ikon share mata hawaye. Abba ya miƙa masa wata leda mai ɗauke da magungunan musulunci yana faɗin, “Ga wannan ɗazun naje na amso maka shi, dan yawan ciwon kan nan naka yana damuna. Ka kula dan ALLAH dayin yanda duk suka rubuta a kuma cigaba da addu’a dan itace gaba da komai muma muna muku ALLAH ya kawo iyaka”.
Ya amsa da Amin tare da masu godiya zuciyarsa a raunane. Ashe haka akeji idan za’a bar gida. Ashe ba mata ne kawai ke shiga cikin yanayin damuwa ba yayinda za’a kaisu gidan aure. Ji yake kamar ya saki kuka kawai ya huta. Amma dai ya daure ya cije da ƙyar yay musu sallama ya fita inda Ahmad ke jiransa. Sai da ya koma cikin gidan yay sallama da su Umma da dama abinda take jira kenan, cikin dabara tai masa hoto batare daya sani ba, dama sanda aka kawo Lulu haka tayi. Koda ya fito inda Ahmad yake sai da suka tsaya akai sallar magrib a masallacin anguwar sannan suka wuce. Basu ƙarasa sharaɗa ba sai da Ahmad ya tsaya yay saye-saye irin na rakkiyar ango, shi dai Smart baice komai ba, hakan yasa Ahmad komawa tsokanarsa wai kodai a samo masa mayafi ya lulluɓa kamar yanda amare keyi idan za’a kaisu. Dan ya lura shima ɗin fa kukan kawai ya rage yayi. Kunnen Ahmad ya kama ya murɗa da faɗin, “Kai wai bazaka daina sa ido ba ko”.
Hannun Ahmad ya buge masa. “Mugu ciremin kunne zakai dan kai ka samu ka tsallake.” murmushi kawai Smart yay baice komai ba. Koda suka iso sai da ya fita ya buɗe gate ɗin sannan Ahmad ya shiga, shi kuma ya rufe sannan ya samesa dai-dai yana fiddo ledojin sayayyar da yayi. “Mawashi ya kamata fa gidan nan a nema maigadi gaskiya”.
Cikin taɓe baki da ƴar harara Smart ya ce, “Yayi me idan an nemosa?”.
“A’a gadi mana, kana ganin ya dace ace kaine zaka dinga buɗe gate da rufewa idan kun shigo ko Madam ɗin. Sannan shi amfanin mutum a gida ko tafiya kukayi baku da ɗar akan barin gidan babu kowa.”
Duk da ya gamsu da maganarsa ta ƙarshe sai cewa yay “Kai share wannan batun muje kazo kayi ka wuce dare nayi”.
“A’a nazo dai nayi na wuce na baka fili kawai zakace malam. Kai jama’a wai kowa da yayi aure sai idonsa ya buɗe, bara dai nazo nai mai yiwuwa, in sha ALLAHU nima bazan ƙetare shekarar nan ba”.
“Da yafi maka”.
Cewar Smart yana murmushi. Daga haka suka ƙarasa cikin gidan. Wani irin ƙamshi mai ratsa zuciya ne ya tarbesu, falo kam ya tsaru iyakar tsaruwa dan Uncle Yousuf da gaske ya zuba dukiya a gidan nan ƴar gaske. Zaune Ahmad ya kai, shima Smart sai ya zauna ɗin yana furzar da iska. Ko yaya zata kaya musu a wannan gida cikin wannan rikitaccen aure mai cike da cakwakiya da ƙalubale oho. Yau dai ga shi da ga shi sai Lulu ƙamshi ƴar balaja’un ogar nan tasa da bata raina abin masifa matsayin ma’aurata. Shi yasan akwai babbar ƙura, idan yace ƙura yana nufin ƙura irinta turniƙewar yaƙi da ko tafin hanunka ganinsa bazai yiwu maka ba…”
“Oh oh tunanin mi kuma ka tafi?”. Ahmad ya katsesa. Iska ya ɗan furzar da sakin ajiyar zuciya. Ahmad yay dariyar shaƙiyanci yana miƙewa. “Ƙalau kake kuwa?” cewar Smart da ke kallonsa. Ahmad ya ɗage kafaɗa da faɗin, “Kafin kowa sanin ƙalau nake tunda gashi na rakoka wajen amaryarka. Ni kaga nayi nan asha angwanci lafiya kar dai a karya gado da safe a kiramu neman kafinta”.
“ALLAH ya shiryeka mara mutunci”. Cewar Smart yana miƙewa shima. Yanzun ma shi ya buɗe masa gate ɗin yana faman jera masa godiya. Dan Ahmad yayi matuƙar ƙoƙari a bikin nan. Ko shine angon sai haka. Sai da ya rufe ko’ina sannan ya sauke ajiyar zuciya da bin ƙofofin ɗakin uku da kallo. Duk da biyu a cikin corridor suke ƙaramin ɗakinne a ware shi kaɗai ɗan nesa da su ma. Zuciyarsa tafi kaisa a corridor ɗin dan haka ya nufi can kai tsaye, tafiya yake tamkar wanda ke jin kasala ko gandar takun nasa, hakan yay matuƙar jagorantar steps ɗin nasa wajen kasancewa a tsare, hannunsa ya kai saman handle ɗin ƙofar, sai ya samu kansa da ambaton sunan ALLAH kafin ya murɗa ya shiga da sallama can ƙasan maƙoshi. Hasken ɗakin ya bashi damar hangota naɗe a tsakkiyar gadon, ya ɗan zuba mata ido na wasu sakanni kafin ya ƙarasa cikin ɗakin da shima keta tashi ƙamshi, yana da ga tsayen ya kira sunanta a hankali, idanun ta buɗe da ƙyar dan bata da nauyin barci, ko abu tasha ta kwanta da wuya kaga barcinta yay nauyin da za’ai abu a kusa da ita bata farka ba. Maidasu tai ta rufe tana wani ɓata rai. Duk da yanda tai ɗin sai bai damu ba ya kai zaune a bakin gadon sai dai nesa da ita kaɗan, koba komai yau ai ita baƙuwarsa ce, ada bai kulata ba ma balle yanzun. Hannunsa ya kai saman goshinta, da zafi sosai alamar zazzaɓi yau ma.
“Yau ma zazzaɓin ne?”.
Kamar bazata kulashi ba sai kuma ta ɗaga masa kai kawai. Iska ya ɗan furzar a hankali. Sai kuma ya ce, “Tashi to kici wani abu sai kisha magani”.
Kalamar magani da ya ambata yasa kanta kawo wuta, cikin gamsuwa da dabarar data zo mata ta tashi zaune da ƙyar tana ƙara cin serious, sai da ta zauna sosai bayanta jingine da gadon sannan ta ɗan kallesa ta kauda idonta, ganin hankalinsa nakan wayarsa yasa taji ƴar nutsuwa dan bata ƙaunar kallo. Cikin ƙara dai-daita plan ɗinta murya a karye ta ce, “Nifa paracitemol bayamin maganin zazzaɓi”.
Ɗan ɗagowa yay ya kalleta, sai kuma ya sake maida idon nasa kan wayar yana faɗin, “Sai wanne?”. Handbag ɗinta da ke bedside drawer ta ɗauka ta zaro wata takarda a bayan zip ɗin ta miƙa masa. “Wannan shi nake sha in dai ina irin wannan zazzaɓin, in ba haka ba bana warkewa da wuri”. Harga ALLAH bai kawo komai a ransa ba tunda shi ba likita bane, dan haka ya amsa takardar, ganin rubutun Doctor ya sashi sake yarda. Sai kuma ya ɗan kalli agogo, takwas da kusan rabi dare baiyi ba. Idanunsa ya maida kanta, ta janye nata da ke kallonsa a sace cike da basarwa. “Ya kamata kici wani abu to kafin na dawo ko?”. A ɗan yatsine ta ce, “Karka damu har ka dawo.”
“Okay”.
Ya amsa mata yana miƙewa. Wani irin daɗine ya ratsa Lulu kamar ta fasa ihu dan farin ciki. Wai yayama akai wannan dabarar baizo mata ba tuni take a wannan bala’in. Zamewa tai ta kwanta tana murmushin da kakan daɗe baka gani ba akan fuskarta dan sai ta gadama take yi.
Napep ya samu ta kaisa har ƙofar pharmacy ɗin data kwatanta masa ana iya samun maganin, koda ya basu takardar yaron saida ya kallesa, amma sai baice komai ba ya dai wuce wajen ɗakko masa maganin. Koda ya dawo da maganin ya faɗa masa kuɗin ya cire daga aljihu ya bashi. Napep ya sake samu ta maidashi gida. Yanzu kam sai da ya rufe ko’ina da ɗaukar abubuwan da Ahmad ya siya musu sannan ya nufi ɗakin. Inda ya barta anan ya sameta, sai dai yanzu ta koma ta kwanta. Duk da taji sallamarsa bata motsa ba har sai da ya kai hannu ya yaye bargon data rufa har kanta. Jikinta har tsuma yake lokacin da ya fiddo maganin da ga leda mai tambarin pharmacy ɗin, amma sai tai ƙoƙarin kannewa.
“Yanzu mi zaki ci?”.
Ya faɗa yana ɗagowa ya kalleta. “Ni bana jin yunwa, naci abu tare da Mamy”. Ta bashi amsa idonta akan ledar nan dai. Bai san wa take cema Mamy ɗin ba, sai dai yanda tai maganar cikin serious ya sashi gamsuwa, sai kawai ya cire maganin biyu ya miƙa mata tare da goran ruwa. Bata musa ba ta amsa tasha. Sannu ya sake mata da tattare sauran maganin ya ajiye a bedside drawer da ruwan. Zamewa tai ta sake kwanciya da faɗin, “Sai da safe”.
Murmushi ya ɗan saki ƙasa-ƙasa. Dan ya fahimci korarsa akeyi. Baice mata komai ba ya tattare sauran ledojin ya fice yana rage mata hasken ɗakin. Ajiyar zuciya ta saki mai ƙarfi, sai kuma ta miƙe zumbur da raka bayansa da harara ta dannama ƙofar key sannan ta dawo. Cikin rawar jiki ta fisgi ledar nan ta zazzage kusan ƙwayoyin maganin biyar a tafin hanunta ta afa a baki batare da ruwa ba. Sai da ta haɗiye sannan ta ɗauka ruwan ta kora kaɗan. Wani irin farin ciki take ji na samun kayan nan cikin sauƙi, sai kawai ta faɗa saman gadon cike da jishaɗi tai juyi ta sake juyawa……..✍️
_(ALLAH ka rabamu da mummunar ƙaddara. Wlhy irin masu ɗabi’ar nan tausayi suke ban. Dan rayuwar kawai suke batare da sun san ina ta dosa ba, idan sukai nisa sai an dage kafin su bari, ku ga dai, kwana biyu batasha ba amma ta koma kamar mara lafiya. Iyaye dan ALLAH mu ƙara dagewa wa ƴaƴanmu, mu bar aibata ƴaƴan wasu idan muka gamsu a irin wannan halin. ALLAH ka shiryar damu😭🙏)._
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣0️⃣
……..Koda Smart ya kai kayan nan kitchen ya adana wanda zai iya lalacewa a fridge sai ya nufi ɗayan ɗakin kasancewar duk yasan sirrikansu, hasalima key ɗin ɗakin na hannunsa dan a rufe yake tun da aka gama shirya masa kaya aunty Saliha ta damƙa masa ko ƴan ganin gidan amarya babu wanda ya leƙa cikinsa. Shima nan ɗin kayane lafiyayyu aka shirya, dan shine ma matsayin master bedroom. Ɗakin yayi ƙyau sosai, komai ya zauna a inda ya dace. Duk da gajiyar da yake ji bai kwanta ba sai ya zare rigarsa da ga shi sai dogon wandon da singlet ya nufi bathroom. Bai jima ba ya fito da alamar alwala yayi, lafiyayyen carpet ɗin gaban gadon ɗakin ya hau dan yin salla. Sallar isha’i yay da shafa’i da wutri. Bayan ya idar yay zaman yin addu’a mai tsayi kafin ya miƙe. Har ya zauna a bakin gadon sai kuma ya miƙe, zuciyarsa ke ayyana masa ya kamata ya binciketa ko tayi sallar isha’i, ya kuma duba ko zazzaɓin ya sauka. Sai dai me, yana taɓa ƙofar ya jita a kulle. Shiru yay yana kallon hannunsa da ke saman handle ɗin, sai kuma ya ɗage kafaɗunsa alamar ko oho ya juya ɗakin da ya fito yay kwanciyarsa dan barci yake ji matuƙa. Dan shi a tunaninsa ko Lulun tayi hakanne dan kar ya nema wani abu a gareta…..
_WASHE GARI_ koda ya tashi sallar asuba sai da ya ƙwanƙwasa mata ƙofa, ganin zai makara saboda ya tashi shima a ƙurarren lokaci ya sashi ƙyaleta ya wuce. Ana idar da sallar ya dawo gidan, ɗakin nata dai ya sake nufa ya ƙara knocking. Lulu da ke kwance a ƙasa ta buɗe idanunta da sukai matuƙar nauyi da ƙyar ta iya miƙewa cikin takaicin damunta da ake tun ɗazun ta nufi ƙofar ta buɗe, dan ta manta ma a ina take, dai da ta ɗan jingina da ƙofar na wani ƴan sakanni sannan ta murɗa key ɗin ta buɗe kaɗan. Da farko bai niyyar shigowa ba, dan haka yace da ita, “Kin tashi kinyi salla ne?”.
“Zanyi”.
Ta amsa masa cikin yanayin muryar maye da tura ƙofar zata rufe dan abun bai gama sakinta ba. Da sauri ya riƙe ƙofar gabansa na faɗuwa, bata da wani isashen ƙarfin dan haka ya samu nasarar shigowa. Yanda ya kafeta da idanunsa da suka kaɗa sukai ja a ƙanƙanin lokaci ya sata zabga masa harara itama da nata dake a juye ta bar masa wajen cikin ɗan tangaɗi na rashin ƙarfi ta je ta faɗa saman gadon a rufda ciki gashinta dake a hargitse ya lulluɓe fuskar tata gaba ɗaya. (Ina ta samu abinda tasha?) Zuciyar sa keta kaikawo wajen son hasasowa amma iya hasashen ya auna a ɗan tsukun lokacin baro gidansu zuwa nan hakan bamai yiwuwa bane, sai dai idan dama tana tare da abunta. Inda take ya ƙarasa ya ɗauki handbag ɗin ta gaba ɗayanta ya zazzage a saman gadon. Babu komai a ciki daya danganci ƙwaya, jakkar ya ajiye cikin furzar da iska sai idanunsa suka sauka kan ledar maganin jiya daya sayo mata, jawo ledar yay ya fiddo maganin, an ƙara ɗiba kusan shida a ciki, ya tsirama maganin ido kallon da yaron pharmacy ɗin ya dinga masa lokacin da ya bashi takardar na dawo masa a rai da zuciya. Tabbas wannan maganin tasha. Kallonsa ya maida gareta ya zuba mata idanu kawai maƙogwaronsa na kai kawo a cikin wuyarsa da ɗan sauri-sauri. Da ga ƙarshe ma sai ya tashi ya fice da ga ɗakin kawai…..
____________________★
Cikin ɓacin rai yake dubansa ganin yanda yake neman haukata kansa. Gaba ɗaya kwanakin nan baida wani aiki sai shaye-shaye tunda ya baro Kano. Ƴar ƙaramar robar giya da ke a hannunsa ya fisge cikin masifa. “Wai mi kake son maida kanka ne kai kuwa MM? Akan mace! Ka zauna ka susuta rayuwarka. Tunda ka dawo da ga kano an kasa gane kanka, ka bar zuwa aiki ka barma fita a gidan nan gaba ɗaya sai shaye-shaye, kana ganin hakan da kake shine zai baka damar samunta? Yarinya sai kace wata autar mata ko hurul-ayni Mtsowww!!!”.
Murmushin takaici MM Atik ya saki sai kuma ga hawaye sharrrr. Ya miƙa hannu zai amshi ƴar robar giyarsa da abokin nasa ya karɓe amma sai ya hanashi. Lips ɗin sa ya ciza da ƙarfi da faɗin, “Bazaka gane ba Asim, duk yanda zan faɗa maka bazaka gane ba. Aure fa sukai mata, aure da wani bani ba. Idan ban mallaketa ba zan iya rasa raina, ina matuƙar sonta da buƙatarta Asim, wlhy da gaske nake ina sonta da gaba ɗaya zuciyata..”
“A haba gyara dai zancenka my man, kana dai sha’awarta. Kai har kasan wata soyayya ne. Ni yanzu Indai dan batun yarinyar nan ne ka nutsu dan ALLAH ka dawo hayyacinka. Ba igiyar aure ba ko ɗaurin kabari sukai mata namaka alƙawarin sai ta dawo taka…”
Wani irin zuba masa ido MM Atik yayi, sai kuma yay murmushi da lumshe idanunsa ya buɗe a lokaci guda, “Asim karka yaudari kanka nima ka yaudarani. Kasan minene aure a ƙasar hausa kuwa?….”
“Mtsoww kafin wannan zamanin yake wani abu a ƙasar hausar, amma a yanzu bana jin wasu matan na tuna matsayin auren, dan ajiyesa suke su shigo barikin ko ƴammatan basu kaisu iskanci ba. Balle ma ita munada hanyoyi kala-kala na kamata a tafin hannunmu. Ko an faɗa maka wani son auren take, to nayi bincike mai zurfi na gane komai har ma yanda aka ƙulla auran. Kai dai kawai ka dawo a hayyacinka kasha labari”. Ya ƙare maganar yana tattare sauran kwalaben giya da su cigarette da shisha da MM Atik ɗin ya baza, sannan ya zo ya kamashi ya kai toilet yasa a ƙarƙashin shower ya sakar masa ruwa. “Malam yi wanka ka cire wannan dattin sai warin hayaƙi kakeyi”. Daga haka ya fice ya barsa.
_____________★
Da mamaki Ammah ke kallon Umma da ke faman murmushi riƙe da basket irin na saƙar kaba ɗin nan mai ƙyau shaƙe da kulolin kayan abinci wai karin kumallo ta shirya za’a kai gidan Smart. Umma data fahimci Ammah zata iya bata matsalafa sai ta sake faɗaɗa fara’arta da katse mata tunani da faɗin, “To kodai banyi dai-dai bane Hafsatu? Dama dai ganin haka akeyi a gidan washe garin da yaro ya tare da matarsa shiyyasa, kuma kinga dai ai ba’a barki da haɗa abinci ba duk gamu cike da gida ko, sai dai kuma naga kamar hakan bai miki ba”.
Murmushi Ammah tayi da ɗan girgiza kanta. Cikin nutsuwar nan tata ta ce, “Ko ɗaya ba haka bane Umman Nasiba, naga kawai an sakaki aiki ne tunda safen nan….”
Caraf Umma ta amshe da faɗin, “Yo minene ALLAH na tuba. Ai an riga an zama ɗaya. Hydar a gidan nan kuma ai ya cancanci fiye da haka. Shi kaɗaine yaron da bai gajiyawa wajen binka har cikin ɗaki ya gaisheka kullum kuma cikin girmamawa da mutuntawa. Bari kiga Huwaila ta miƙa musu tunda tace zata gane gidan lokaci na ƙara ja”.
Murmushin ƙarfin hali kawai Ammah ta saki da faɗin, “To ALLAH ya saka da alkairi”.
Umma ta amsa da “Amin”. tana ficewa
“Anya wannan al’amarin Hafsatu ba akwai wata a ƙasa ba. Matar da tunda aka fara bikin nan ta kasa ɓoye hassadarta ce zata girka abinci akaima Babangida kuma a barta?”. Addah Rukayya ce mai maganar cikin jimantawa. Kafin Ammah tace wani abu Gwaggo Sa’adah ta fito a ɗaki ita da Addah Suwaiba. Har rige-rigen faɗin, “Wannan yaudara ce akwai wata a ƙasa” suke su biyun. Adda Suwaiba ta cigaba da faɗin, “Babu ma wani batun ai mata kawaici magana ta gaskiya fa, kawai a dakatar da su ba ga Hawwah can na musu girkin ba shi kuma ai yaya da shi?. Matar da bata taɓa ƙaunarki ba tun da jajayen sawu sai yanzu ne zata ƙaunaceki Hafsatu, ai daga ji ma kasan akwai ƙulunboton data shiryama abincin. Ita idan yaran nata sunyi auren barinku take ku girka abinci ku aika musu ko sai ke, naga Yalwati ma ta aurar da yara maza har uku a gidan nan ai batai mata hakan ba dan tasan bama yarda zatai ba sai ke sarkin kawaici”.
“Addah ni a ganina ku barta, idan ma wani sharrin take nufi ai ALLAH bazai bata nasara ba. Ballema ni sai nakega kawai dai tayi hakane saboda tujarar da malam yay mata jiya da dare”.
Gwaggo Sa’adah ta ce, “Humm Addah kenan. Yau ya fara mata tujara ne da har hakan zai sakata saduda. ALLAH ki yarda ke dai akwai wani abu a ƙasan kawai. Bakuma zamu gane hakan ba sai anje ankai musu abincin sun cutu mudawo muna dana sani”.
Duk da zuciyar Ammah ta sake raunana sai bata iya sake cewa komai ba, sai ƴan uwan natane ke cigaba da tattaunawa dan na cikin ɗaki ma duk sun fito. Gwaggo Sa’adah ce ta nufi kitchen inda Hawwah ke girka karin kumalon da za’a kai gidan Smart. Cikin sa’a ta iske ta kammala tana kan zubawa ne. “Yauwa kin haɗa ne Hauwa’u?”. “Eh Gwaggo” cewar Hawwah. Gwaggo Sa’adah ta ce, “Yauwa to sannu, bara na turo su Asma’un suyi su tafi rana nayi”. Da ga haka ta juya ta koma. Ƙwafa Umma dake leƙarsu ta window tayi, jitake kamar ta fito ta shaƙe wuyar Gwaggo Sa’adah. Oho dai tata ƴar aiken ai harta wuce. Kafin kuma su isa ta tabbatar Hydar da matarsa sunci nata abincin. Tai wata ƴar dariyar gatsa-tsa tana barin window ɗin har ɗiyarta Ismaha na kallonta. Amma sai ta basar dan tasan wacece Ismaha da ɗan banzan jan wa’azin tsiya………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣1️⃣
……..Ƙarfe kusan tara Lulu ta tashi da ƙyar a dalilin kaɗawar alerm ɗin ƙaramin agogon da ke a side drawer ɗinta da ya gallabeta tun takwas. Amma nauyin da jikinta yay mata yasata kasa kasheshi ko ta tashi har zuwa yanzu da ya sake buga taran. Ƙaramin tsaki taja da ɗan kai hannu tana lalube, sai dai sam babu ma alamarsa kusa da itan. Tamkar wadda aka ƙwalama kira sai kuma ta miƙe zumbur, yau fa ya kamata ta shigar da case ɗin mijin matar can court, dama tai alƙawarin sai ya kwana bakwai a police station su Shu’aibu sunci mata ubansa gwargwadon iko sannan, yau kuma kwana bakwan cif. Wayoyinta ta shiga nema, sai kuma ta tuna sunafa hannun Uncle You nan kuma gidan da aka kawota jiya ne. Ƙaramin tsoki taja da dafe kanta da yay mata matuƙar nauyi, dole ta sakko a gadon cikin ɗan tangaɗi kaɗan sai dai bana mayen bane na nauyin jikine dan abinda tasha ɗin sun saketa sai abinda ba’a rasa ba. Bayi ta shiga ta tsaya ƙarƙashin shower batare data cire komai ba daga jikinta ruwa ya fara sauka mata a haka. Ajiyar zuciya ta dinga saki a jajjere, sai da ruwan yay mata sharkaf ta gamsu ta ƙara komawa garau da take buƙata sannan ta fara zame kayan jikin nata ta fara wanka. Tana kammalawa ta jefa kayan a injin wanki dan komai na ƴar gata an ajiye mata shi, sai da ta gamsu sun wankun sannan ta ciresu ta maida indai zai busar. Sai ga kaya ras ta fitar sannan ta fito. Tana buƙatar waya domin kiran Zainab sakatariyarta da kuma su Shu’aibu ɗan sanda, dan haka ta fito da ga bedroom ɗin nata daga ita sai rigar wanka da towel ɗin data naɗe gashinta da take son ruwan data jiƙashi da shi ya naɗe. Sautin muryarsa yana raira karatun Alkur’ani cikin suratul An’aam daya karaɗe corridor ɗin ya sata gane yana a ɗakin dake kusa da wanda take. Sai da ta sake gyara yanayinta dan karma ya kawo mata wani raini sannan ta murɗa handle ɗin ƙofar ta shiga kanta tsaye ba batun neman izini, sallama ma sai da ta gama shiga tayita ciki-ciki. Ƙamshin shower gal dana haɗin turarrukan wankan da masu gyara mata jiki suka shirya mata na musamman ne ya fargar da shi shigowar ta, dan cikin abinda baifi sakans ba ɗakin ya gauraye da masifaffen ƙamshinta. Kasancewar yazo inda ya kamata ya tsaya ya sashi rufe Alkur’ani ya ɗago ya kalleta. Kanta ta ɗauke daga kallon da take masa, shima sai ya janye nasa idanun yana ajiye Alkur’anin. Cikin izzar nan tata da gadara ta ce, “Ɗan bani aron phone ɗinka na kira Uncle You ya bada nawa a kawo min”.
“Kinyi salla?”.
Ya faɗa maimakon amsa mata abinda tazo nema. A yamutse tana balla masa harara ta ce, “Ina ruwanka. Ka bani aron waya idan zaka bani”.
“Idan kina buƙatar waya kije kiyi salla. Shin ke bakiji kunya ba a wannan shekarun naki ace sai an tuna miki abinda zai kusantaki da UBANGIJINKI, banbanci kafiri da musulmi shine sallah, duk wanda yabar salla baida maraba da kafiri, sannan duk wanda yabar salla zai iya aikata kowanne irin mummunan aiki, salla itace abinda za’a fara bincika mana a cikin ayyukanmu ranar sakamako, yin salla akan lokaci na ma masifu katanga da samunmu. Salla na ƙaramana kwarjini a idon al’umma da cikar kamala. Taya mai barinta zai samu waɗan can tagomashin dana lissafa wanda kaɗanne da ga cikin nasarorin da mai salla ke samu. Yinta zai baki damar yima mahaifiyarki addu’a da nemar mata rahamar UBANGIJI, sai ruhinta ya kasance cikin sallama tai alfahari da haihuwarki da jin bata bar bayan a banza ba. Mawaddat babu ruwan mutuwa da yanzu kika fara rayuwa, tana ɗaukar ɗan cikin ciki ma tabar uwa, alokacin da kike jin ke kin fara rayuwa wani ma a ranar aka samar da cikinsa. Ki dawo cikin hankalinki ki koyi darasi a duniya ba sai duniya ta shirya koya miki ba. Dan ita ɗayan biyu ce. Ko ka koya a yayin da take koyar da waninka, kota koyar da kai a lokacin da guri ya ƙure maka. Zaɓi ya rage naki”.
Da ga haka ya tura mata wayar ya miƙe yay wucewarsa toilet. Harara kawai ta bisa da shi ƙasa-ƙasa. Dan gaba ɗaya jitai kamar an danne mata baki a sanda yake maganar. Bakin ta taɓe da matsawa ta ɗauka wayar tasa ta fice abinta. Sai dai tana komawa ɗakin nata ta zauna a bakin gado da nufin kiran Uncle Yousuf hakan ya gagara. Maganganunsa ne suka shiga dawo mata, musamman akan yima mahaifiyarta addu’a kuma zatai farin ciki da ita daya faɗa, samun kanta tai da kiƙewa zumbur ta nufi toilet, babu jimawa sai gata ta fito da alamar alwalar tayi. Wardrobe ta buɗe ta ciro abaya ta saka tare da naɗa gyalenta a kanta ta kabbara sallar.. dai dai nan ya shigo ɗakin shima, dan haka kawai zuciyarsa ta kasa nutsuwa harya fara cire kaya zai yi wanka ya fasa ya biyota dan yaga zatayi sallar. Karo na farko zuciyarsa ta tsarga ganin yanda take salla babu wani bin ƙa’idojinta yanda ya kamata. (Tofa wata sabuwa) ya ayyana a zuciyarsa da ɗunbin takaici. Ashe dole abubuwa suke rikicema yarinyar nan dan babu nutsuwa ko nagarta a cikin al’amarin ibadarta. Tabbas rashin tsaida ibada tamkar wani dafin allura ce a jikin ɗan adam mai karya masa garkuwar nagarta da ɗaurasa akan laifuka. Ashe al’amarin nata ya gawurta da yawa har haka. Zafin rai da takaicin iyayenta ya sake mamaye masa zuciya, domin fa in har ɓera da sata to a bincika itama daddawa nada wari. Shin mi mahaifinta da matar babanta dama Uncle Yousuf keyi haka har balagaggiyar yarinya mai shekaru da yake da tabbacin sun haura ashiri amma bata iya salla ba? Amma a ilimin boko da anyi magana zata iya bugar ƙirji ta kira kanta mai ilimi. Oh ALLAH a wane irin zamani muka tsinta kammu da tarbiyya ke neman kufcewa iyaye saboda soyayyar ƴaƴansu?. Wannan al’amari ya tayar masa da hankali matuƙa, ya tuna lokacin suna yara, idan lokacin salla yay sukaƙi barin wasa suje suyi sai dai kaji saukar tazbahar Ammah a jikinka kawai. Idan ko bakayi ba ranar ko kulaka batayi sai tace ita bazatai magana da wanda yafi son shiga wuta ba. Amma yau sai ga shi wadda ke amsa sunan matarsa bata iya salla ba. A hankali ya jingina da ƙofar yana mai harɗe hannayensa a ƙirji da lumshe idanunsa abubuwa masu yawa na masa kaikawo a zuciya, lallai akwai aiki, dan yaƙine babba garesa akan yarinyar nan, shi duk ma sai yaji tausayinta ya ƙara kamashi..
A ɓangaren Lulu tunda ta idar idanunta ya sauka akan Smart kamar wani mayan ƙarfe. Sai da taji gabanta ya faɗi musamman da abinda ya faru jiya ya shiga dawo mata a rai, amma sai ta basar tama miƙe tana naɗe abin sallar. Sam Smart shi bai san da ta idar ba. Dan idanunsa a lumshe suke ya afka duniyar tunani. Samun kanta tai da tsura masa idanu, yayinda kalaman Nadiya na waccan ranar na dawo mata a zuciya. Kamar wadda aka tsawatarwa sai kuma ta ɗauke idanunta cikin yamutsa fuska tana jan tsaki. Duk da bai san mi take jama tsakin ba saukarsa a tsakkiyar kansa ya sashi ɗagowa cikin nutsuwar nan tasa ya buɗe idanunsa a kanta.
“Gadin na miye?”.
Ta faɗa cikin ƙarfin hali dan ba ƙaramin tasiri idanunsa keyi a duk sassan jikinta ba. Maimakon bata amsa ɗauke kansa yay, hakan kuma sai ya tunzura mata zuciya. Ta buɗe baki zata fara masifar tata yay gyaran murya kaɗan, kamar zata share sai kuma dai ta jiyo ta ɗan kallesa cikin harara tana ƙoƙarin warware gashinta. Ido suka haɗa ta mirrorn ta balla masa harara ta ɗauke nata. Shima ɗauke nasan yay ya maida kan gashinta mai tsaho da alamun samun gyara ya sashi yin wani ƙyau na musamman da sheƙi duk da a jiƙe yake a yanzu. Knocking gate da ake da ɗan ƙarfi ya sashi haɗiye maganar da yay yinƙurin yi. Agogon dake a ɗakin ya kalla sai kuma ya buɗe ƙofar ya fita. Ƙaramin tsaki yaja lokacin da ya fito harabar gidan sosai yaji bugun ƙofar babu ƙaƙƙautawa, sai da yasa key ya buɗe sannan ya zare sakatan. Da sauri Huwaila taja baya tana sissine kanta. Sai da ya gama kallonta ita da kwandon hannunta sannan ya matsa mata fuskarsa na ƙara tsukewa, dai-dai nan napep ta tsaya a ƙofar gate ɗin, dakatawa yay da ga yunƙurin rufewar da yake saboda hango Asma’u na fitowa a Napep ɗin. Fuskarta da murmushi ta ƙaraso garesa tana faɗin, “Yaya ina kwana”.
“Lafiya Lau” ya amsa mata idonsa akan kayan hannunta, itama kallon hannun tayi har sannan fuskarta da murmushi ta ce, “Yaya abincinku n…..” sai kuma ta kasa ƙarasawa saboda hango Huwaila da tai a ƙofar shiga falon ɗauke da kayan abinci itama, da sauri ta kalli Yayan nata kamar zatai magana dan ita bata san da zuwan Huwaila ba. Ganin yay gaba abinsa ya sata bin bayansa batare data faɗi abinda ke bakin nata ba. Kallon juna sukai ita da Huwaila da ke hararta ta ƙasan ido, Asma’u ta ɗan girgiza kanta cikin basarwa ta ce, “Adda ai ban san nan zakizo ba da mun taho tare”.
“Zaku shigo ne ko zaku tsaya surutu”. Smart dake kaiwa zaune cikin kujera ya faɗa. Shiga sukai da sauri, kowa ya ajiye kayan hannunsa suka gaishesa. Amsa musu yay da kulawa, sai kuma Asma’u cikin zumuɗi ta ɗora da faɗin, “Yaya ina auntyn?”. Ɗan jimm yay sai kuma ya nuna mata hanyar bedroom ɗin da Lulu ke ciki.
“Yaya dan ALLAH barci takeyi?”.
Kansa ya sake girgiza mata nan ma. Miƙewa tai, kafin ma yace wani abu harta kusa zuwa ɗakin, ƙoƙarin dakatar da ita yay dan shi dai yasan wacece matar tasa, kuma baya buƙatar ƴan uwansa su fara sanin wacece itan su tun a yanzun, sallamar da Asma’u tai da ɗan knocking ƙofar ya katse masa tunani.
“Asma’u!”.
Ya kira sunanta kamar a kasalance, amsawa tai da “Na’am Yaya”. Tana jiyowa………✍️
(😂Lulu karki bamu kunya dan ALLAH)
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣2️⃣
…….Dai-dai nan Lulu ta buɗe ƙofar ita kuma waya a kunne ta tana magana da Uncle Yousuf cikin shagwaɓa akan a aiko mata da wayoyinta. Miƙewa Smart yay ya nufosu, sai dai yana isowa Lulu da batama lura da shi ba ta riƙo hannun Asma’u suka shige ciki tana mata murmushi. Turus ya ɗan tsaya yana bin ƙofar da kallo, sai ma ya rasa wane irin tunani zai yi. Sai kawai ya ɗan furzar da isa ya nufi ɗakin daya kwana al’amarinta na ƙara ɗaure masa kai, ya fahimci gane ainahin yarinyar nan sai an shirya.
Huwaila da ke kallon komai ta cika tai fam, dan ita babu abinda zuciyarta ya bata sai wulaƙantata da nuna mata wariya. Wayarta ta ɗauka tai kiran Umma, bugu ɗaya kuwa ta amsa, daga can cike da zumuɗi Umma ta ce, “Ya ya kin ɗebo ko?”. Sosai Huwaila ta tunzura baki gaba, idanunta akan hanyar corridor ɗin nasu kamar zata saki kuka ta ce, “Umma bayan munafukar yarinyar nan itama tazo, gashi can ya jata sun shige ɗaki wajen matar tasa sun barni ni kaɗai a falo, dama tunda ya buɗen ƙofar yake min kallon banza kin san shi dai da baƙin halin tsiya, balle yanzu yana ganin ya auri ƴar masu kuɗi kamar yafi kowa a gidanmu.”
Ƙwafa Umma tai da ƙarfi zuciyarta na sake ƙuntata, cikin fusata da jin haushin lusarancin Huwailar ta ce, “To ke bazaki tashi ki bisu ba. Kije duk ma uwar da akeyi a ɗakin ayi da ke. Ki kuma tabbatar kin kwaso min abinda na sakaki”. Ƙitt ta yanke kiran batare da Huwaila ta sake samun damar cewa wani abu ba. Tasan hanlin Ummar su sarai akan jarabar tsiya, dan haka ta miƙe ta nufi inda taga Asma’u ta shiga. Ba knocking ba komai balle aje batun sallama ta afka musu. Asma’u da ke gyaran gado tai saurin jiyowa, hakama Lulu da ke waya da Sakatariyarta Zainab yanzu idanu ta zubama Huwailar.
“Kai Adda Huwaila ALLAH har kin ban tsoro shigowa haka ba sallama”. Asma’u ta faɗa cikin jin takaici sai dai ta tausasa harshenta. Harara Huwailar ta zuba mata da taɓe baki ta nufi sofa ɗin bedroom ɗin mai azabar ƙyau da ɗaukar ido ta zauna, itama sai Asma’un ta watsar da ita ta cigaba da gyara gadon cikin takaici. Harta kammala ta shiga toilet shima dan ta gyara Huwaila na cigaba da harare-harare, sai dai fa ɗakin ya mata masifar ƙyau, ji take inama a cikin ƴan ɗakinsu ne suka samu wannan duniyar haka.
Lulu kam tun kallo ɗayan datai mata bata sake ba tana cigaba da wayarta da Zainab da kuma gyara gashinta data kammala busarwa, so take sai ta kammala taji wace ita da kuma dalilin shogo mata ɗaki haka ba knocking. Asma’u data fito daga Bathroom alamar ta kammala ta yafito da hannu, koda ta iso batare da tayi magana ba ta miƙa mata ribbons da yimata nuni da gashinta alamar ta ɗaure mata. Amsa Asma’u tai da murmushi akan fuskarta, ta shaƙi fitinannen ƙamshin da gashin keyi ta lumshe idanu tana tattarosa cikin hanunta. Dai-dai nan Smart ya shigo ɗakin da sallama. Yayi masifar ƙyau cikin wani kwantaccen yadi da ya sake fiddo nagartarsa ta cikakken bahaushen arewacin Nigeria nutsatstse, daga ita har Asma’un ya zubama ido, sai kuma ya ɗan kalla Huwaila da ke gefe ta baje cikin couch tana ta wani faman hura hanci, sai dai shigowarsa ta sata ɗan nutsuwa dan tasan halinsa sarai.
“Ku tashi mu wuce ku kuma ko?”.
Ya faɗa babu alamar wasa tattare da shi. Asma’u ta ce, “To Yaya can gidan zaka kaima”. Kansa ya ɗaga mata kawai batare da yace komai ba, amma sai Lulu da ke ɗan kwallonsa ta cikin mirror ta juya kujerar tana dubansa da ƙyau tare da janye wayar kunnenta alamar ta kammala. Kallon ido sukaima juna, kowanne ya janye nashi cike da basarwa. Ƙasa-ƙasa ta ce, “Please ka barmin Auta anan dan su Afrah ma na zuwa kawo min phones ɗina”.
Zuba mata idanu yay sosai da alamar mamakinta, dan shi dai bai san yaushe ta fara son mutane haka ba da har ma tasan ana kiran Asma’u da Auta. Maimakon bata amsa sai ya dubi Huwaila da Asma’u. Da sauri suka fice dan dama Asma’u ita tayi niyyar yin hakan, Huwaila ce dai dake kallonsu ta ƙasan ido bata da wannan niyyar. Lulu da ke kallon yanda yaran ke rige-rigen ficewa ta wani taɓe baki, “Kai kowa ma sai ka nuna masa halinka ne, jibi yanda yara ke fita kamar zasu ci da ka”.
“Oh ni har wani hali ne da ni kuma wanda ban sanshi ba?”. Ya faɗa cikin ɗan ɗage gira ɗaya da ƙanƙance idanunsa. Nata tai saurin ɗaukewa da ƙara taɓe bakin ta koma ta juya ga mirror ɗin batare data bashi amsa ba. Ƙarasa takowa yay jikin mirror ɗin shima ya ɗan jingina tare da ɗaukar wayarsa ya duba dawa-dawa tai kira. Ganin number Uncle Yousuf da dama yana da ita, data Zainab da itama dai yana da itan dan tun randa ya kaita gida ya amsa saboda wataran. Ya ɗan ji nutsuwa dan shikam yanzu ya fahimci sai yayi takan tsantsan, tunda har jiya tai amfani da shi wajen sayo mata ƙwaya batare da ya fahimci komai ba dole ne ya nutsu ya fahimci duk wani dabarun su. Iska ya ɗan furzar kaɗan da gyara tsaiwarsa da ƙyau sai kuma ya fara magana a hankali tare da maida hankalinsa sosai ga kallon yanda take tufke jelar gashin bayan ta sharceta da comb. Yana matuƙar son gashi a jikin mace, dan haka natan ke matuƙar ɗaukar masa hankali.
“Zanje na gaida su Ammah na dawo bazan jimaba, sai dai ki sani kar fita ta ta baki damar aikata wani abu daban, dan shaye-shaye babbar hanyace ta maida ɗan Adam baya akan dukkanin nasarorinsa da kima da mutuncinsa. A duk inda mai wannan ɗabi’ar yake zakaga baida farin jinin al’umma, kowa bai san raɓarsa balle huɗɗa da shi da ga sanda aka fahimci yanayi. Shi a karan kansa kuma yakan rasa damammaki da yawa na cikin burinkansa ko nasararsa ta duniya da lahira. Misali ga barin salla, da wahala a samu mai wannan ɗabi’ar da tsaida salla akan lokacinta, hakan kuma babban naƙasu ne ga rayuwa. Karatun Alkur’ani, ambaton ALLAH da sanin mi rayuwa take ciki kota dosa duk dama ce dake kufcewa a hannunsa. Ga ɗiya mace in har tana wannan ɗabi’ar hanya mai sauƙi ce a samu damar keta mata mutuncinta. Shin mi kika rasa a rayuwa na ni’imomin ALLAH da bai miki ba, miyasa ki ka zaɓi gode masa ta wannan hanyar? Miyasa kika zaɓi sakama iyayenki da wannan tukuycin da duk iyayen da suka fuskanci yaransu nayi basu da sauran nitsuwar zuciya, ki tuna kema uwa ce wataran. Bazance miki ki kiyaye ba, dan ban isa hanaki ba, sai dai ki sani wannan itace ɗabi’a ta biyu da bazan ɗauka ba bayan barin salla. Ki zauna kiyi nazari. Ga break fast can su Asma’u sunzo da shi. Nima yanzu zan dawo sai na karya a nan ɗin, ina son yin abu mai muhimmanci ne acan”. Da ga haka ya nufi hanyar fita abinsa batare da ya ko waiwayo ba balle yaga halin da tasirin da maganganunsa sukayi gareta. Lulu da tun fara maganarsa abu ya tokare mata maƙoshi ta raka bayansa da kallo wani shegen takaicinsa da mamakin gadarar nan tasa da yake son fara bayyana mata a fili. Wai mi wannan mutumin ke nufi da ita ne? To duk abinda ya shirya ita a shirye take da mafiyinsa su zuba ita da shi a gidan nan ɗan halak ka fasa, ina ruwansa da rayuwarta….
Dawowar Asma’u da kayan shara ɗakin ya maidota hayyacinta. Ta kalleta tana ɗan waro idanu waje. “Ya barki ne?”. Cikin zumuɗi Asma’u ta bata amsa da “Eh, amma yace yana dawowa zan wuce. Shiyyasa zanyi sauri na shashshare miki aunty dan shifa Yaya baya magana biyu”. Yanda ta ƙare maganar da ƴar shagwaɓa ya sanya Lulu sakin murmushi. “Uhhm kudai autocin nan ko’a ina sai kun nuna hali. Kinga bar batun sharar nan karki wahal da kanki nace su Amrah su taho da Iya tabawa zatazo duk ta gyara ko’ina”.
“A’a aunty ki kirasu ma kice su barta basai sunzo da ita ba. Zan gyara yanzun nan dan nan ma sharane kawai da gogewa ya rage. Nifa kin san ina son aikin gida sosai, shiyyasa su Aunty Bilkisu idan suna jin lalacinsu har zuwa suke su ɗaukan na musu hutu koda Ammah zataita ƙorafi ne sunta lallaɓata kenan”.
“Uhhmm sannu busy body ke baƙya gajiya ma kenan. To nidai bazakimin aiki ba, amma zanso Ammah ta bari ki dawo mana nan kinga na samu abokiyar hira ko.”
“Tab aunty Ammah bazata bari ba, ba irin nacin da mijin Aunty Bilkisu baiyi ba kan a basu ni amma taƙi ita da Abbah. Amma ke ƙila taji kunyarki ta yarda ko weekend nake zuwa dan tasan dai halin Yaya bai son yin magana sai yaso, kina buƙatar abokiyar hira”.
“Zan gwada na gani to, ALLAH yasa su bani, bari na shirya naci abinci ina ɗan jin yunwa kaɗan-kaɗan, kema ajiye kayan sharar nan Please”.
Magiya Asma’u tai taima Lulu har sai da ta barta tai aikin nan, dan danan kuwa ta tsaftace ko’ina ta baza kayan ƙamshi. Itako tana zaune a falo tana tsakurar abincin da su Asma’u suka kawo, sai dai tana buɗe wanda Huwaila ta kawo ta maida da sauri ta rufe saboda jin ƙamshin korin da aka zambaɗa a miyar fankason ta dakar mata hanci, sam ita bata ƙaunar kori a abinci shiyyasa ma idan har an saka batacin sa komai son da take masa. Sai kuma ma akai rashin sa’a fankasu ba abincinta bane shima, duk randa ma Iya Tabawa tayisa a gidan to ita sai dai ai mata wani abun, hakama idan taje gidan Uncle Yousuf ko gidan Grandpa ta tarar anyi bataci, bata son su shi da tuwo sam musamman miyan yauƙi ko wani taga yanaci sai zuciyarta ya hau tashi. Wanda Asma’u ta kawo ta buɗa, a hankali ta saki ajiyar zuciya ganin lafiyayyen yam balls ne a kular farko, ta biyu farfesun naman kaza ne yanata tashin ƙamshin attaruhu da albasa. Sai jug irin mai riƙe zafi ɗin nan ɗauke da kunun gyaɗa da yay ƙyau yanata ƙamshi har da su ƙwa-ƙwa a cikinsa. Sai shayi a flaks da yaji kayan ƙamshi shima, anan kam ajiyar zuciya ta sauke harda sakin guntun murmushi ta zuba kunun gyaɗar da farfesu kaɗan ta fara tsakura tana bin Asma’u da keta aikinta a nutse da kallo da sauraren labarin da take bata akan yanda suke matuƙar jin daɗin abinda take yi game da case ɗin fyaɗe. Haka kawai jin ƙaunar yarinyar take a ranta, balle jin abinda take faɗa na yanayin da suke shiga na jin daɗi har itama tana burin zama lawyer kamarta……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣3️⃣
…….A ɓangaren Smart kam suna isa gidan sashen Abba ya nufa domin gaidasa, yayinda Huwaila ta shige ciki fuuu tana ƙunƙuni. A falo ta iske Umma zaune suna karin kumallo da sauran ƴan uwanta da ƴaƴansu da duk ke shirin wucewa gida a yau tunda biki dai ya tashi. Umma ta bita da kallo kamar a firgice, sai dai kasancewar bata son tace wani abu a gaban sauran yaran ya sata ƙyafta mata ido ta cigaba da cin abincinta. Amma Huwaila sai ta dinga ƙunƙuni, da ga ƙarshe dai ta fara bama ƴan uwanta labarin ƙarya da gaskiya akan wai an mata wulaƙanci a gidan Smart, sun shige ɗaki sun barta, yanzu kuma yace Asma’u ta zauna can ita kuma ya taso ƙeyarta sun dawo. Da yawansu sun hau sun zauna. Sai Ismaha ce dai ta ce, “Humm Huwaila gaskiya ban yarda ba. Koda ace hakan da kika faɗa ma ta faru sai dai idan yanada manufarsa, kowa dai yasan Yaya Hydar a gidan nan kan rashin nuna bambanci a tsakaninmu da ƴan ɗakinsu. Da dai Yaya Salim kikace yayi hakan ko musa miki bazanyi ba…” tana gama faɗa ta tashi tai ficewarta. Cikin ƙanƙanin lokaci falon ya kaure da ka-ce-na-ce, kowa na faɗin albarkacin bakinsa. Da wannan damar Umma da hankalinta sam ba’a jikinta yake ba ta miƙe tana kama hannun Huwaila suka shige uwar ɗaka.
“K lafiya? Ina abinda na aikeki yi na ganki hannu rabbana”.
“To Umma ya kike so ki ganni, a gabanki fa na faɗi irin wulaƙanci da akai min a gidan can”.
“Ke tafi can wawuyar banza da wofi, kin ko san muhimmancin abinda na turaki yi da zaki dawo min da wani shirmenki na banza. Wai ke ko Huwaila yaushe ne zakiyi hankali a rayuwarki. Ƙanwar-ƙanwarki Asma’u har ta fiki wayo amma ke gallaƙeƙiyar budurwa da ake shirinma aure baki son ciwon uwarki ba….”
“To wai ni Umma ya kike so nayi dan ALLAH. Ni Wlhy ko ƙyallin wani kayan da suka saka jiya suka cire ban wani gani ba a gidan. Tunda kina ganin banyi miki ƙoƙari ba sai kije da kanki ai”. Tana gama faɗa tai waje abinta. Duk irin kiran da Umman ke ƙwala mata ko waiwayenta batai ba. Sai ma jiyo muryar Smart da tai alamar ya shigo gaishe ta. Sai dai yanda taji ƴaƴan nata na gaishesa a gatsine ya sata fita wuff dan taga suna neman ɓata mata shiri, saboda Malam Na-zuru ya jaddada mata a waya ɗazun da safe sai fa ta rage nuna abinda ke ranta a garesu, musamman ma matar tasa tai duk yanda zatayi ta shiga jikin yarinyar hakanne zai sakasu cin nasara cikin sauƙi. Cike da fara’a ta amsa gaisuwar da Smart ke mata tana tambayar ya baƙuntar sabon waje da amarya. Kansa a ƙasa cikin jin nauyi da girmamawa ya ce “Lafiya Lau tana gaishe ku”.
“To madalla ALLAH yay muku albarka. Kamayi ƙoƙari ai da ka fito tunda safe haka banyi zaton yau zamuga idonka ba a gidan nan kwata-kwata.”
Shi dai murmushi kawai yay yana miƙewa batare da ya bata amsa ba ya fice abinsa. Sashen Ammah ya shiga dan ya gaisa da mama da Aunty Amarya. Nan ma dai zama yay suna gaisawa da dangin mahaifiyarsa da ke ta jansa da kiransa babansu babansu. Daga haka suka sake ɗora masa da nasiha mai ratsa jiki tare da addu’oin zaman lafiya mai ɗorawa da zuri’a mai albarka. Bai jima ba sosai Adda Suwaiba tace ya tashi yaje yabar matarsa dan ma Asma’u nacan. Daga haka yay musu sallama ya fito bayan sun ɗanyi magana da Ammah a gefe ya kawo kuɗin jikinsa na gudunmawa da ya ɗan sassamu ya bata akan ta basu suyi kuɗin mota. Daga haka ya juya ya tafi akan zuwa anjima zai dawo kafin su tafi gidan su Lulu godiya ta al’ada da ango kanje da abokansa gidan dangin amarya washe garin tashin biki…..
Har lokacin da ya shigo gidan Lulu na zaune tana tsakurar abincin nan, yayinda Asma’u ke ƙarasa saka turaren ruwa a carpet ɗin falon da labuloli. Ɗaga kai kawai tai ta kallesa ta maida kan abincinta batare data amsa masa sallamar ba. Sai Asma’u ce ta amsa tana masa sannu da zuwa cikin girmamawa. Amsa mata yay da kansa kawai. Da yake hankalinta ba’a kansu yake ba ita bama ta lura Lulu bata amsa masa sallama ba. Ta kammala ta maida turaren a inda ta ɗauka Lulun na mata sannu cikin murmushi. Ta gefen ido yake kallonta da mamakin yanda take sakema Asma’un. Baki ya ɗan taɓe batare da ya kalla Asma’un ba ya ce, “K zoki bani abincin nan na karya”. Amsa masa tai da to Yaya, sannan ta nufi kitchen ɗin ɗakko masa plate kamar yanda ta ɗakkoma Lulu ɗazun. Sai lokacin ya dubi Lulun a kaikaice, cikin deep voice ɗin nan tashi a dakensa ya ce, “Ke baki iya amsa sallama ba balle sannu da zuwa ko, amma kin iya tasa abinci kina ci”.
“Sauƙin ma bakai ka bani ba balle kamun gori shishshigi master”. Ta faɗa tana balla masa harara. Lips ɗin ta dake motsawa a hankali yabi da kallo, sai kuma ya ɗan cije nasa da ɗauke kansa yana jin wata irin kasala na sake saukar masa fiye data barcin da yake ji. Bai sake magana ba saboda fitowar Asma’u, ta jawo basket ɗin gabansa tana buɗe kulolin da faɗin, “Yaya mizan zuba maka bayan kunu dan nasan dai shikam ba canji”. Ƙaramar hararar data sata saki siririyar dariya ya sakamar mata, sai kuma ya nuna mata yam balls ɗin da faɗin, “Karki sakama kunun komai”. Da to ta amsa masa, sannan ta zuba komai yanda ya kamata kuma dai-dai adadin da tasan zai cinye dan shima yam balls ɗin ma masoyinsa ne. Lulu da ke satar kallon abincin ta gefen ido ta ce, “Hu’umm kuma duk cinyesa zakayi?”. Yanda tai maganar da ɗan waro Luluu eyes ɗinta waje tana riƙe haɓa ya bama Asma’u dariya, sai dai ta danneta da ƙyar ta tashi ta fice da ga falon gaba ɗaya taje waje tai abarta son rai.
Smart ya ɗan laɓe baki batare da ya kalleta ba ya fara cin abincinsa da faɗin, “Mi kike tsoro ne a cikin cin abincin nawa? Kina gudun kar ki gagara ɗaukata ne?” ya ƙare maganar da ɗago idanunsa da take kira na macizai ya zuba mata su. Baki ta taɓe cikin masa kallo mai kama da harara ta ce, “Kamar ya? Miya shafen da nauyinka?”.
A karan farko ya saki wani makirin murmushin da aduk sanda yayisa yake tunzurata dan tafi kwallonsa a murmushin rainin hankali ya cigaba da cin abincinsa. Siririn tsaki taja da ɗauke kanta itama ta cigaba da shan romon farfesun da yaci ace tama manta ta gama ci. Amma ina gayu da yanayinta yasa anata tsakurarsa, ga shi yamata daɗi matuƙa ta yanda ta gagara ajiyesa. Duk da yaji tsakin nata bai sake yin magana ba ya maida hankalinsa ga cin abincin harya kammala zai tashi, sai lokacinne itama take kammalawar. Asma’u ya ƙwalama kira, ta amsa da ga waje dan ta gama zagaye gidan ne tana jin daɗin kallon flowers ɗin da aka ƙawatashi da su. “Zoki wuce gida” ya faɗa yana miƙa mata ɗari biyu. Lulu Asma’u ta kalla cikin shagwaɓe fuska, itama Lulun shi take kallo, ta ce, “Kamarya tazo ta tafi? Nan fa zata kwana”. Yanda take maganar itama kamar a shagwaɓa-shagwaɓa ya sashi kallonta. Sai kuma ya ce, “A ina ɗin zata kwana? No karma ku fara abinda bazaku iya ƙara sawa ba, common Malama ɗakko hijjab ɗinki ki wuce gida, wannan abincin ki tafi da shi a bama wani dan nan dai bacinsa za’ai ba”. Da ga haka yay wucewarsa hanyar bedroom. Sum-sum Asma’u ta nufi kwanikan da suka kammala cin abincin ta tattara zata kai kitchen sannan tazo ta wuce dan tasan shifa baya magana sau biyu. Takaicin wannan nuna isar tasa ya saka Lulu miƙewa a fusace tabi bayansa. Burumm ta shigo ɗakin dai-dai ya zare rigarsa zai cire wandon, amma sai ya dakata ya tsaya kallonta.
“Malam wai kai miyasa kake son dinga juya mutanene kamar wasu ƴaƴanka?”.
Kallonta kawai yake yi batare da yace komai ba. Aiko sai ta sake fusata da takaicinsa ta ce, “To babu inda zataje”.
“Idan kece sama da ni kenan”.
Ya faɗa yana ƙara tsatstsareta da idanu. Itama a tsiwace ta ce, “Oh da mika ɗauki kanka?”. Karo na biyu ya saki murmushi, dan shi kam ƙarfin halinta tunba yanzu ba dariya ma yake bashi. A hankali ya tako zuwa gabanta daf, ta wani yamutsa fuska tare da matsawa baya tana hararsa, sake matsawa yay shima ta matsa itama, shima ya bitan dai, a masife ta ce, “Miye haka wai?”.
“Ina son nuna miki abinda na ɗauki kaina ɗin ne Madam” yay maganar dai-dai suna danganewa da bango idanunsa cikin nata. Yanda suke daf-daf ga hannunsa da ya tokare a bangon ya bashi damar dabaibaye ta da ƙyau har tanajin numfashi na neman mata wahalar shaƙa dan in ma ta shaƙa ɗin ƙamshinsa ne iskar da kawai take iya zuƙowa ya sata faɗin, “Aliyu bana son iskanci da raini fa. Dalla matsa min”..
“Haba Madam! K bakiji kunyar faɗar sunan ba haka gatsal sunan mijinki ne fa”. Yay maganar da sake ranƙwafowa yay mata rumfa ta yanda jikinta ke neman fara rawa. Amma sai ta dake dan bata yarda itafa yaga gazawarta ba. Hannu tasa ta turashi amma ko gezau, sai ma wani lumshe idanun da yay ya sauke akan hannayen nata da ke a saman jikinsa. Da sauri ta janye tana jan tsaki da faɗin, “In ma abinda banzan zuciyarka ke faɗa maka kenan to ka goge, dan tamkar kana mafarki ne a gaɓar da ake gab da tashinka da ruwan sanyi, wannan auren baida maraba da wasan drama ɗan son banza phone store”.
Idanunsa ya lumshe da buɗewa a lokaci guda yana cafko hanunta dan shirin duƙewa take tabar wajen. “Haba Madam ya kuma zaki wuce ban nuna miki abinda na ɗauki kan nawa ba?”.
“Aliyu!!”.
Ta sake faɗa da ƴar tsawar takaicin kiranta Madam da yake yi dana goga jikinsa a nata.
“Uhmm Madam”.
Ya amsa mata da wata irin kasalalliyar muryar son sake ƙular da ita yana sake kusanta fuskarsa gab-gab………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣4️⃣
……..Ƙarshen kuma firgita Lulu ta gama kaiwa, sai dai kafin tai wani yunƙuri a matuƙar bazata taji saukar lips ɗinsa masu sanyi akan tausasan nata masu sheƙi da ƙamshin lipgloss ɗin data ɗan saka, cin abinci ma yasa duk ta shanye rabi. Iyakar rikicewa da firgici Lulu ta shiga, gashi ya mata ritsawar da ko iya motsa kanta ta gagara yi balle tace zata iya ƙwacewa. Shi kansa da yayi ne domin kawai tabbatar mata ba drama ɗin data ambata ɗin bane jiyay gaba ɗaya jininsa na yamutsawa, dan karo na farko kenan a rayuwarsa da haka ta faru tsakaninsa da mace. Da ƙyar ya iya juriyar shafe minti guda sannan ya sake mata lips amma bai matsa da ga jikin nata ba, sai ma magana da ya fara cikin kunnenta muryarsa a wani irin sarƙe duk da jarumtar son hana hakan bayyana da yake nunawa. “Waya gaya miki baƙo na kwana gidan sabbin aure ne? Ai sai ya jiyoma kansa abinda zai hanashi barci, bar yarinyar mutane ta tafi gidansu girmanta bai kai ba. Sannan ki rage ɗaukar kanki sama can ƙololuwa, dan a wannan fadar Aliyu Hydar shine ZAKIN KI. Fassara SARKIN KI Mawaddatan’warahmah Isma’il Ibrahim Jiƙamshi”. Ya ƙare maganar da ɗanja baya yana wani kashe mata ido ɗaya ya bar wajen gaba ɗaya.. Suɓul numfashin Lulu ya nema barin jikinta. Takaici ne, baƙin ciki ne. Mamaki ne bata sani ba. Abinda kawai ta sani wannan itace rana mafi abin takaici da koma baya da tazo mata a tarihinta. Bakin illiterate driver ɗinta ne cikin nata, ya zuba mata yawunsa ta sha fa a cikin cikinta. Wayyo ALLAH shike nan tata ta gama ƙarewa….
Kamar Smart ya san mi take tunani, dai-dai yana hawa gadon ya wani lashi lips ɗinsa da faɗin, “1-0 kenan, amma fa yawunki akwai daɗi Madam. Ina fatan nawa ma akwai ɗanɗano na musamman irin wanda iyali zasu so. Dama na faɗa miki jahilin baƙauyen nan fa ɗan takife ne, ki guji masa gatsali dan bajin magana yake ba. kije ki sallami yarinyar mutane inba haka ba na tashi na ganta a gidan nan ita ranta zai ɓaci, ke kuma zakisha yawun baƙauyenki”.
Harara ta watso masa da faɗin, “Shash….” bata ƙarasa ba ya yunƙura zai tashi. Da gudu ta fice kuwa tana nunashi da yatsa da faɗin, “Wlhy sai na koya maka hankali. Maye!”.
Komawa yay ya kwanta yana mai lumshe idanunsa da sakin ƙaramar dariya. A hankali ya furta, “Na samu promotion da ga illiterate velleger zuwa MAYE kenan”. Sai kuma ya kai hannunsa saman lips ɗin nasa ya shafa yana jin wani abu na masa yawo a cikin jini har yanzu. “Ko mima ya kai ni, ni Aliyu Madam ce fa”. Ya sake faɗa yana wani ɓata fuska kamar gaske, sai kuma yaja filo ya ɗaura a saman face ɗin sa da sake faɗin, “ALLAH ya shiryeka Aliyu wannan abun kunyar da ka tafka fa wa ogarka”.
(😂😂Ɗan manni, amma ka kwana da sanin idan muka tashi ramawa sai ka raina kan ka malam🥱 Tom😏🚴).
_________★
A hankali Mommy ta jinjina kanta tare da sakin ajiyar zuciya na ɗunbin mamakin Daddy a karo na babu adadi. Kallonta ta sake maida wa garesa har yanzu yana a yanda yake zaune da tagumi hannu bibbiyu. Abincin data ajiye masa kusan tsawon awa guda har ya ƙandare shayin ko ya koma kamar ruwan sanyi. A tsakanin shekaranjiya zuwa yinin jiya yanayinsa na nuna kewar barin Lulu gidan ne kamar yanda suma duk sunji hakan a ransu, amma da ga daren jiya zuwa safiyar yau yanayin nasa sai ya ninka ko barcin kirki bata tunanin yayi, da farko tayi tunanin ko baya jin daɗin jikinsa ne. Amma koda ta tambayesa amsar da ya bata sai taji ta girmi kunnenta. Tun cikin daren take tunanin anya kuwa mijin nata kuma ɗan uwanta lafiya lau yake? Dan al’amarin nasa kuma ya fara wuce makaɗi da rawa. Ita bama ta fatan ko Yousuf yaji wannan taɓargazar tasa a wannan gaɓar dan abin kunya ne na gaske. Ajiyar zuciyar ta sake saukewa, sai kuma ta miƙe a nutsenta ta koma gefensa ta zauna. Karo na farko akan al’amurin Lulu ta fuskancesa da son tausasawa da nuna masa goyon baya ɗari bisa ɗari. Hannunsa ta kamo cikin nata tana ɗan murmushi da faɗin, “Yaya kayi haƙuri kaci abincin, ka kuma kwantar da hankalinka bari na shirya sai naje gidan na duba mana Mawaddat ɗin, duk da dai inaji a jikina yaron nan bazaiyi abinda zamuce ALLAH wadarai ba. Amma nima zuwa yanzu zuciyata tafi gamsuwa da naje na dubatan tunda babu waya a hannunta balle mu kira, tura yara kuma bazai bamu abinda muke so ba.”
A karo na farko shima Daddy ya dubi Mommy ɗin da tausasawa a akan lamarin Lulun. Murya a sanyaye ya ce, “Kina ganin baza’ace munyi ba daidai ba Kareema, kin san fa masifar Yousuf akan yaron nan daban ce, na rasa wane irin so yake masa da bai son ace yayi ba dai-dai ba. Ni kuma wlhy ina tsoron ya illatamin yarinya a banza tunda dai ba taɓa auren nan yay ba balle muce zai kamanta dattako”.
Shike maganar amma Mommy ita kejin kunyar, amma sai ta danne ta biye masa cikin sake kwantar da murya. “Na fahimceka Yaya, dan samarin nan na yanzu kam rawar kai ya musu yawa, duk da shi dai a fuska kamar nutsatstse amma ba’a yabon ɗan kuturu. Yanzu dai kaci abincin bara na canjo maka sai naje na gano ɗin ko yaya kace?”.
“Shike nan, in dai kina ganin babu matsalar kije ɗin, dan nima dai hakan zai fi sama min kwanciyar hankali. Sannan dan ALLAH ki lallaɓa Yousuf ya bata wayoyinta dan mu dinga jinta akai-akai”.
“Karka damu idan yazo anjima zan masa magana. Bari na kawo maka abincin kaci namaje na dawo da wuri kafin yazo gidan”.
Kai ya gyaɗa mata, ita kuma ta tashi ta fice idanunta na cika da ƙwallar tausayinsa. Yayinda zuciyarta ke faman kai kawon anya kuwa mijin nata yana lafiya? Dan ita dai gaskiya a wannan gaɓar ta fara jin al’amarin nasa da girma, wanan wace irin makauniyar soyayya ce? Haka fa idonsa yay masifar rufewa akan mahaifiyar yarinyar nan a lokacin tamkar wanda baya a hayyacinsa. Anya kuwa basuyi kuskuren nutsuwar fahimtar al’amarin nan ba a bai-bai tun a shekarun baya? Kuɗi kam na iya canja mutum fiye da abinda Daddy yayi a kan Mawaddat, sai dai akan ƴarsa Mawaddat kuma fa? Idan ance soyayyar mahaifiyarta ce ta dawo kanta gaba ɗaya ai abin nasa na neman wuce makaɗi da rawa kuma, sannan ko sanda ya auri Mawaddat yanada abin hannunsa, bayan auren nata ne dai ya sake bunƙasa za’ace, gaskiya tana buƙatar yin dogon nazari a wannan karon fiye da wanda sukeyi a baya game da shi. Koda ta kawo masa abincin ma lallaɓashi tai tayi sai gashi yaci, ta sake lallaɓashi yay wanka ya kwanta dan yau kam babu alamar zaije office ma. Ita kuma ta shirya ta fice a gidan kamar gaske gidan Lulun zataje. Yo ita zata biye masa ne su zama ɗaya miya ja mata wannan abin kunyar. Gidan Uncle Yousuf tai tafiyarta, tai sa’ar samun shima yau ɗin bai fita office ba wai zai ɗan huta a gida…….
____________★
Duk yanda Lulu taso lallaɓa Asma’u ta zauna hakan bai yiwu ba, dan ita dai Asma’u tasan wanene yayan nasu. Haƙuri tai ta bama Lulu akan ai zataje ta dawo kawo musu abincin rana. Amma yanzu idan bataji maganarsa ta tafi ba ya fito zai iya zane ta. Mamakin Lulu sai ya sake ninkuwa, irin wannan tsoronsa da suke ai abin yayi yawa. Amma idan yasan wata ai bai san wata ba. Sai tayi duk yanda zatai Asma’u ta dawo gidan nan da zama kafin cikar sati ukun da zatatai a cikinsa kodan ta tabbatar masa itama ɗin ba kanwar lasa bace. Da ga haka tabarta ta wuce. Kasancewar gidan shiru ita kuma bata son kaɗaici yana tayar mata da hankali ya sata miƙewa ta ɗan zazzagaya, duk da kasancewar gidan ƙarami sosai, dan ko sashen masu aikinsu ya fisa girma bai hana gidan birgeta ba. Balle ma an sake ƙawatashi da kayan da aka zuba mata, wanda har mamakin sakasu tayi ita da zatai zaman sati uku. Sai dai batace komai ba akan hakan. Ta ɗan jima a waje tana shan iska sai kuma ta koma ciki, bedroom ɗin ta, a ranta tana raya gara ta ɗan sha abubuwanta ta kwanta itama tai barci, sai dai me koda ta duba babu ledar maganin ma gaba ɗaya. Shiru tai alamar tunanin ko ta ajiyesu a wani waje ne, kai ina a bedside drawer ta barsu. Da sauri ta buɗe drawer ɗinsa amma babu alamar su, maganganunsa na ɗazun bayan zuwan su Asma’u ne suka shiga dawo mata, to ko ya fahimci abinda tai jiyan. “Wayyo ni” ta faɗa tana dafe kanta. Dama fa tayi matuƙar mamakin jin ya ɗakko topic ɗin nan, sai dai kafin tai masa tambayar da tai niyya ya fita ya barta. “Mutum nan maye ne, ya akai yay saurin ganoni” ta sake faɗa tana faɗawa saman gadon da jan tsaki. Bataso haka ba gaskiya, dan tana ganin ta samu hanya mai sauƙi da zata dinga samun abinda take so cikin sauƙi tana wasa da hankalinsa. “Mugun kai fal gadara da ƙauyanci sai shegen wayo kamar ɗan dila” ta sake faɗa cikin nuna takaici. Da ga haka tai shiru lamo abinda ya farun yanzu babu jimawa a tsakaninsu na sake dawo mata. Tsaki taja mai ƙarfin masifa ta sake juya kwanciyarta dan sam bata son tunawa, dan duk ƙaƙarin aman data dinga yi bayan barowarta ɗakin nasa batai ba, sai ɓigewa tai da yin brush kusan sau huɗu amma hakan bai hanata cigaba da jin saukar lips ɗin nasa a nata ba har yanzu. Tsaki taja tana tunzura bakin gaba. Da ga haka ALLAH ya taimakata barci ya kwasheta mai ƙarfi. Dan koba komai akwai gajiya da ƙarancin barcin na kwana biyu a tattare da ita………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣5️⃣
……..Cike da matuƙar ɗoki Asma’u ta isa gida, kusa da Ammah ta zauna da ke kallonta ganin yanda take ta faman washe haƙora. “Auta lafiya kuwa irin wannan washe baki haka ko suruki na samu?”. Adda Sa’adah ta faɗa cike da zolaya. Su Adda Suwaiba da ke ta shirin wucewa gidajensu suma dai duk idanu suka zubawa Asma’un. Dariyar ta sake faɗaɗawa tana ɓoye fuskarta a jikin Ammah da faɗin, “Kai Gwaggo nifa ba haka bane, zan faɗama Ammah albishir ne”.
“A to muma sai a faɗa duk muji ai”. Cewar Gwaggo Sa’adah. Asma’u dai na dariyarta ta ce, “Gwaggo dama fa zan sanarma Ammah ne matar Yaya itace lawyer ɗin da take so ɗin nan mai taimakon mutane musamman akan harkar fyaɗe”.
Kallonta Ammah tai da sauri, dan haka cike da zumuɗi Asma’u ta sake faɗin, “Wlhy Ammah da gaske nakeyi. Barrister Mawaddat Jiƙamshi ce matar Yaya, dama tun shekaran jiya nake ta mamaki dana ga kamanninsu yayi yawa duk da ban taɓa ganin waccan a zahiri ba sai a tv, sai banyi magana ba sai yau dana tabbatar”.
Wani irin abu ne mai sanyi ya shiga ratsa zuciyar Ammah ta shiga sake tsarkake sunan ALLAH maji roƙon bayinsa. Tun a randa ta fara ganin yarinyar nan ana hira da ita a gidan tv akan wani case data cimmawa na fyaɗe har yarinyar ta kamu da cuta mai karwa garkuwar jiki da wanda yay mata fyaɗen ya goga mata a ranta taji inama ace ɗiyarta ce ita, ko kuma Aliyu ya sameta a matsayin mata. A ranar tai addu’a da fatan idan hakan zai iya kasancewa kuma ya zama alkairi ALLAH ya tabbatar, idan kuma har matarsa ce. Amma da ga baya sai ta cire hakan a ranta sakamakon jin yarinyar ɗiyace ga babban hamshaƙin mai arziƙi nan Alhaji Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. Ta cigaba da ƙaunarta kawai a ranta da mata fatan alkairi a rayuwa. Tuna wannan al’amari ya sakata jin ratsawar wannan al’amari mai sanyi har zuciyarta na harbawa da sauri-sauri, tabbas wannan shine ɗaya da ga cikin alkairan son mutum domin ALLAH, dan ita kam taso yarinyar nan domin ALLAH ne……
★★….
Tunda Mommy ta fara magana Uncle Yousuf ya zuba mata idanu kawai yana kallonta har sai da takai aya. Ta ƙare da faɗin, “Gaskiya Yousuf zuciyata ta fara raya min wani al’amari mai girma. Anya kuwa babu lauje cikin naɗi a wannan al’amarin. Kasan mu mata munada wani hali na rufewar ido a duk sanda muke son ganin buƙatarmu ta biya akan abinda muke so. Ka tuna randa marigayiya ta fara ganin Yaya kuna tare, kuma kaine da kanka ka sanar min tunda yay mata kallo ɗaya ya watsar da lamarinta har kuka baro gidan a wancan lokacin bai sake kulata ba”.
“Tabbas anyi haka aunty Kareema, amma miya alaƙanta wannan abin kunyar da yake yi yanzu da wancan?”.
“Ba zamuce sunada alaƙa ba, ba kuma zamuce basu da shi ba. Amma inaji a jikina wannan soyayyar mai zafi da yakema Mawaddat bata lafiya bace.”
Murmushi Uncle Yousuf yay da gyara zamansa. Ya ce, “Aunty Kareema ban katseki ba ko ƙin fahimtarki anan, amma ina roƙonki karki sakama zuciyarki komai game da abinda Yaya keyi da tunanin wani. Lafiyarsa lau ya kuma san mi yake yi sarai. Akwai dai abinda yake ɓoyewa shiyyasa yake kaffa-kaffa da Mawaddat, dan ba wai tsantsar soyayyar bace ba kawai. Abu na biyu tausayin rasa mahaifiyarta tana laɓuɓuwa ma ya taka rawar gani a kansa. Kin san mu maza munada wani abu akan ƴaƴan mu musamman idan ya kasance mahaifiyar yaro bama tare da su, sai mu dinga jin wadda ke riƙe da su zata cuta musu ne kawai. Shiyyasa zakiga maza da yawa suna samun saɓani da matansu akan ƴaƴan da uwarsu ta fita a gida, kota rasu ta bari.”
“To haka ɗinne kuma. Amma inaga ya kamata ace munsan abinda yake ɓoye manan ko hakan zaisa mu fahimcesa”.
“Karki damu zamu sani, lokacin mu sani ɗinne dama baiyi ba, ina kan bincike yanzu haka ma”.
“To Alhamdullah ALLAH yasa muji alkairi.”
Da Amin ya amsa mata, da ga haka suka cigaba da tattauna al’amarin Daddy ɗin har zuwa wani lokaci kafin tai musu sallama ta koma gida. Ta samu Daddy na ramuwar barci da ya gagara yi daren jiya, bata tashesa ba har sai da ya tashi da kansa sannan ta labarta masa abinda ya sakasa nutsuwa kamar yanda suka tsara da Uncle Yousuf. Murmushi yay da faɗin, “Ashe yaron nan nada hankali har haka”.
Dariya Mommy tayi kawai batace komai ba. Shima sai bai sake bi takanta ba ya tashi ya shige bayi fuskarsa ƙawace da murmushi…
__________★
Gab da Azhar Smart ya tashi a barcin da yay, yaji daɗin yin barcin kuwa sosai, dan haka ya watsa ruwa da ɗaura alwala yasa jallabiya ya fice massalaci batare daya nema Lulu ba. Sai da aka idar da salla ya dawo gidan sannan ya nufi ɗakinta. Baccinta take hankali kwance, beauty face ɗinta ta sake yin wani fayau kasancewar babu ɗigon kwalliya, hatta lips ɗin ma yanzu babu ko lipgloss ɗin a jikinsa. Samun kasan yay da tsira mata idanun nasa na tsawon mintuna, tabbas ita ɗin ƙyaƙyƙyawace, sannan tana cikin jerin mata masu tsananin kula da jikinsu ta hanyar gyarashi kwaf-kwaf a kowane motsi. Ga izza da gayu da duk wani cikakken namiji bai isa mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa ba, “Sai dai akwai kauɗi da masifa kuma ba” ya faɗa a fili yana ɗan taɓe baki da ƙarasawa gaban gadon ya tadata. Idanunta ta buɗe a hankali ta saukesu kansa. Yanda ya ɗan ranƙwafo kanta ya sata zabura, dan yanayin ya mata kamar wani abu da ya shuɗe a baya. Tashi yay shima tsaye da kyau yana girgiza kansa. Fuska ba wasa ya ce, “Tashi kiyi sallah”.
Harararsa tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa saboda yanda yay masifar kafeta da idanunsan nan da bata ƙaunar ya zuba mata su, dan duk wani ƙarfin gwiwar ta sai ya sare taji komai ya kufce mata. Dama fitsari take ji dan haka ta sauka a gadon tana wani yamutse fuska ta nufi bathroom ɗin. Sai da ya bata ɗan lokaci sannan yabi bayanta, anyi sa’a kuwa zata fara alwala.
“To alwalan ma a gabanka zanyi?”.
“Haka ya kamata, ya kuma dace, dan hakki ne a kaina sanin ibadarki da komai naki a yanzun”.
“Kai a wa?”.
“Mijinki”.
“Kana son shigarmin rayuwa da yawa”.
“A ciki nake tsunduma ma ai”
“Mafarki kenan”.
“Ni da ke duk a ciki muke, mai rabo a cikinmu sai ya fara farkawa ya fuskanci reality. Yi alwala lokaci na tafiya”.
“Al….”
Sai kuma ta kasa ƙarasawa saboda tuno abinda ya faru ɗazu a ɗakinsa saboda faɗar sunan nasa. Sai kawai ta ɓige da maka masa harara cikin ƙunƙuni ta furta “Zan koya maka hankali sannu-sannu”.
Duk da yaji bai tanka ba, dan ya gaji da magana haka nan. Itama sai tai ƙwafa ta juya ta fara alwala. Shi dai yana kallonta harta kammala zata miƙe ya ce, “Dakata. Mawaddat ba haka ake alwala ba sam. Akwai kura-kurai matuƙa a cikin wadda kikayi. Dan haka ina son ki bani hankalinki nan duk abinda nayi kiyi, yanda ake alwala shine. Da farko yin niyya a zuci sannan ki ce Bismillahi, sannan ki wanke tafukanki na dama da na hagu kowanne sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki kurkure bakinki ki zubar da ruwan sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki shaka a hanci ki fatar shi ma sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki wanke fuskarka gaba ɗayanta sau uku, ki lura cewa wanke fuska yana farawa ne tun daga farkon goshinki har izuwa karkashin haɓarki, wato kusa da makoshi a tsayinta kenan, a faɗi kuma tun daga gefen kunnen dama zuwa gefen kunnen hagu. Sannan ki wanke hannu tun daga tafuka har zuwa gwiwar hannu na dama da na hagu shima sau uku. Sannan ki ɗebo ruwa ki yi shafar kai wato a tafin hannu ki shafo tun daga farkon goshi har ki kai ƙeya sannan ki sake dawowa farkon goshi. Sannan shafar fatar kunnuwa na dama da na hagu. Sannan ki wanke ƙafafu na dama da na hagu tun daga tafin ƙafa har izuwa gwiwar ƙafa. Ina fatan kin fahimta, amma zan fara sai kiyi duk yanda zanyi”.
Batace komai ba, sannan bata nuna zata ƙiyi ba. Dan ita dai tun maganarsa ta ɗazun akan mahaifiyar ta ya matuƙar sanyaya mata jiki, tsaf ta dingayin yanda yake yi har suka kammala, har cikin ransa yaji daɗin rashin gardamarta a wannan gaɓar. Dan haka ya ɗora da faɗin, “Akwai addu’a bayan kammala al’wala. Zan koya miki ita bata da wahala bata kuma da tsaho, sai dai ba yanzu ba sai na kammala shirina akan hakan. Muje kiyi sallarki”.
Komai batace masa ba yanzu ma tai wucewarta ta fita shi kuma yabi bayanta yana jin wani kaso na takaicin abinda ya faru daren jiya akan sayen magani na raguwar masa a zuciya. “Yanzu bamu da isashen lokacin da zan miki filla-filla akan yanda ake salla, amma zan nuna miki kaɗan a ciki kafin mu fara karatu na musamman akanta.” bai damu data amsa ba ya shiga nuna mata da faɗa mata abinda zata iya fahimtarsa a yanzun, nan ma dai batace komai ɗin ba har ya kammala ya bata izinin kabbara sallarta. Da ga haka ya samu waje ya zauna yana kallonta har ta idar. Ya dubeta zaiyi magana game da addu’a ganin har ta miƙe da ga sallamewa kira ya shigo wayarsa. Ahmad ne, dan haka ya ɗaga yana kaiwa kunne. Shaƙiyanci sosai Ahmad ke masa da ga can, har sai da ya sashi furta, “Ɗan sa ido ina ruwanka to. Kai ni karma kazo min gida ka tsaya nan nazo na sameka mu tafi”. Ƙaramar dariyar da ta saka Lulu kallonsa yayi kaɗan saboda jin abinda Ahmad ya faɗa da ga can. Sai kuma shima Smart ɗin da ya miƙe zai fice taji yana furta, “Irinku ne masu takurama sabbin aure da zarya har sai an cinye kayan gara da k….” daga haka ya fice bata ƙarasa ji ba. Baki ta taɓe kaɗan da ajiye sallayar tana sauke ajiyar zuciya da bata san dalili ba, da ga haka ta ajiye batunsa tai zaman dirshen a kan gado ranta fal tunanin cases ɗin dake gabanta. Dole ne ma gobe idan ALLAH ya kaimu ta fita office, kwana kusan tara yau fashin yayi yawa ai haba. Bata sake jin motsin Smart ba har sai da Mubarak ya kawo abincin rana. Lokacinne ya shigo ɗakin cikin shirinsa da alama fita zaiyi dan yaci wani faran shadda ƙal harda hula baƙa, ƙamshi yake mai sanyi ya fito a angonsa dai kai tsaye. Da ga bakin ƙofa ya dakata yana faɗin, “Ga lunch can an kawo ni zan fita su Ahmad na jirana”.
Baki ta taɓe kawai batare da tace komai ba. Shima sai bai sake cewa koman ba ya juya yay ficewarsa dan ya fahimci ƴan izza da masifar ne yanzu a kanta. Shi kuma bashi da wani isashen lokacin biye mata a yanzun……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣6️⃣
……..Ya samu su Ahmad na jiransa a ƙofar gida shi da wani cousin brother ɗinsa babban fan ɗin Smart akan ball, da yake kusan sa’ansu ne shima sai suke zumunci sosai duk da shi Smart ɗin yana jajja baya kamar yanda halayyarsa take na rashin sakewa da mutane. Ko Faisal yayi fushi sai kuma ya dawo dan matuƙa Smart ke burgesa a filin ƙwallo, damma ƙaddara ta hana komai gudu ai da yasan yanzu Smart na cikin manyan ƴan ƙwallo da Nigeria ke alfahari da su. Sun gaisa tare da zolayarsa irin na abokai musamman ma Ahmad da ya tasashi gaba sosai kafin su wuce Smart na roƙama Ahmad shiriya. Gidan Daddy suka fara zuwa. Inda suka sami tarba ta musamman da ga Mommy da su twins da basu koma ba. Bayan sun gaisa da Mommy sukai godiya tai musu iso falon Daddy da ya riga yasan da zuwansu. Ya ɗan sake musu fuska harda jansu da hira duk da sunata faman sinne kai musamman ma Smart. Dan koda aka kawo musu abin sha da ruwa da kayan motsa baki Faisal da Ahmad ne kawai suka sha ruwa. Shiko babu abinda ya taɓa. Wasa-wasa sun share kusan awa ɗaya da rabi kafin su baro gidan da wasu kayayyakin Lulu da Mommy ta saka Mubeen kai musu akan sai zuwa gobe idan ALLAH ya kimu za’a kai mata sauran kayan. Da ga nan gidan Uncle Yousuf suka nufa. Anan ɗin ma dai tarba suka samu ta girmamawa ga Aunty Saliha. Uncle Yousuf kuwa babu ruwansa zama yay cikinsu tamkar aboki tunda su duka ukun babu baƙonsa, gara garama Smart ɗin, amma su Ahmad ai tun suna dajinen majina ya sansu. Anan ma sun jima dan har sai da aka kira sallar la’asar sannan suka fito tare da Uncle Yousuf ɗin zuwa massalaci. Bayan sun dawo basu shiga ciki ba sai mota tunda dama sunyi sallama da Aunty Saliha. Anan ma dai an bada wasu kayan Lulu da wayoyinta da laptop da Uncle Yousuf ya amshe. Bayan sun baro nan Smart yace ma Ahmad yana son zaije yaga Malam tunda zuwa gidan Baba da sukai niyya ya rushe sakamakon sanar dasu Baba yayi tafiya Legos da Uncle Yousuf yayi. Ahmad yace babu damuwa. Sun nufi Yakasai wajen Malam Nasirudden. Sunyi sa’ar samunsa kuwa a gida bai fita ba. Bayan sun gaisa Ahmad ya janyo Faisal cikin dabara suka fito suka bar Smart tare da malam ɗin.
Malam Nasirudden da ya fahimci akwai magana ya dubi Smart cikin murmushi da kulawa ya ce, “Idon Aliyu ango ne haka a waje, kai da ya kamata ace kana can gida sai bayan wata ɗaya ka fito”.
Murmushi mai bayyana hakwara Smart ya saki a karo na farko, cikin sinne kai ya ce, “ALLAH ya gafarta malam idan hakan ta kasance ai kwa zaneni matsayinku na iyaye”. Dariya shima malam yayi da faɗin, “Ina ai idan hakan ta faru mun san lafiya ce ta ɓoye ka ai Malam Aliyu. Ya amarya da gajiyar biki?”.
“Alhamdullah Malam”.
“To Masha ALLAH, ince dai ba jikin bane ba ko?”.
“A’a malam jiki kam Alhmdllh, dan duk yau banji ciwon kan nan ba. Wani abu ne mai muhimmanci ya kawo ni dan ina buƙatar ƙarin haske da shawara”.
“To Alhmdllh ALLAH ya ƙara lafiya mai albarka. Ina saurarenka mike tafe da kai?”.
Zama Smart ya gyara yana sauke ajiyar zuciya da furzar da iskar bakinsa. “Malam akan ita matar tawa ne nake neman shawara. Kasan yanda al’amuran rayuwar nan suke tafiya a wannan lokaci musamman tarbiyya da ke neman zama wani babban ginshiƙi mai wahalar aiwatarwa ga iyaye ko riƙewa ga mu ƴaƴan, wasu zakaga iyayen nata iya bakin ƙoƙarinsu amma sai su fuskanci jarabawa a cikin ƴaƴan wasu su fanɗare, ko kaga tun fil’azal iyayen ne ma basu bi hanyoyin isar da tarbiyyar yanda ya kamata ba saboda soyayyar yaran. Wannan matsalar tana matuƙar tasiri akan addini da wasu ɗabi’un da takai a yanzu hatta ɗiyanmu mata na shaye-shayen abubuwan mayen nan a cikin gidajen iyayensu ko a gidan aure. Wasu sanadin abokai, wasu samari, wasu kuwa wani daliline kan jasu zuwa hakan. Karna jaka da nisa, ita matar tawa ta tsinta kanta a irin wannan halinne, sannan ba shaye-shaye ne kawai matsalar ba, hatta a ɓangaren ibada tana da matuƙar raunin da zan iya cemaka komai ma bata sani ba, saboda koda tasan wani to babban dalilai ya shafesu da ɓoye abinda ta sani ɗin. Kaina gaba ɗaya a cikinkushe yake yinin yau ka bani shawara dan ALLAH, dan ko mahaifana bana son su fuskanci wannan matsalar game da ita balle sauran ahalina saboda bana son mutuncinta ya samu rauni ko yaya a zukatansu”.
Numfashi mai nauyi Malam ya sauke yana mai jinjina kansa. “Tabbas kai ɗan halak ne Aliyu, sannan ka matuƙar birgeni na kuma sake ganin kimarka a cikin idanuna. Domin ba kowa ALLAH ke azurtawa da irin zuciyarka ba a wannan ƙarnin. A koda yaushe, a ko wane irin kuskure mutanenmu sukan dubi mai wannan akin abin ƙyama, abin hantara, abin gudu, abin zinɗe, abin shune, a tunaninsu suma wayonsu ne ya hanesu da aikatawar ko ya hani nasu zuri’ar. Muna mantawa itafa rayuwar tamu gaba ɗayanta ma jarabawace, ba kuma lallai ne abinda ya kasance jarabawar waninka kai ya kasance taka ba. A duk sanda kaga gazawa ga wanin ka ba dandalin gulmarsa ya dace ka buɗe ba, da zunɗensa ko shunensa ya dace kayi ba idan zai gifta, ba ƙyamatarsa ya dace kayi ba ko hantara. Nema masa shiriyar UBANGIJI ya cancanta da tausasa masa a duk lokacin da rayuwarsa ta raɓi taka ko wani dalili. Wlhy Aliyu mutane da yawa sukan kasa gane cewar bakunansu ko ayyukansu ke jefa musu ƴaƴa cikin wata musifar. Zakaga kana iya bakin ƙoƙarin ka akan tarbiyyar yaranka, ALLAH kuma ya baka su nutsatstsu da ilimi yanda ya kamata, amma dare ɗaya yaro ya canja alƙiblarsa ka rasa daga ina matsalar take. Matsalar tana a tare da kai, bakinka shine matsalarka, ayyukanka sune matsalarka. Ɗan wancan dake famɗare ya gitta ka zunɗeshi da bama abokan zamanka labarin ai wancan yaron da kuke gani gagararrene, watsatstsene fanɗararre, baida aiki sai shaye-shaye, baida aiki sai bin ɗiyan mutane, baida aiki sai ɗauke-ɗauke. Ciki ta zubar babu adadi bar ganinta a cikin hijjab ɗin can karuwar gida ce, jibi yarinyar can babu abinda ta iya sai shigar banza, ta kwaile fata da bilicin ƴar isaka tafi ƙarfin iyayenta. Laifin uwarne ko ubanne basu bashi ko bata tarbiyya ba….. Waya gaya maka tsaiwarka akan tarbiyyar yaro ce kawai ke tsare maka shi ɗan uwana ko ƴar uwata? Muna mantawa akwai jarabawa, muna mantawa akwai ƙaddara, muna mantawa ƙyaƙyƙyawan furucinmu ga ɗiyan wasu kanyi tasiri ga namu ɗiyan, mummuna kanyi tasiri ga namu ɗiyan suma. A duk fa lokacin da ka ambaci ALLAH yayima wane albarka, ya shiryar da shi, sai kaima mala’iku suce Amin tare da kai da zuri’arka baki ɗaya. Idan kace ALLAH ya wadaran wane fanɗararre taƙadari ɗan iska, sai mala’iku su amsa da Amin tare da kai da zuri’arka baki ɗaya. To ashema yima wani ƙyaƙyƙyawar addu’a ko furuci tamkar kanka kayimawa kenan ko, shiyyasa nace maka harsunanmu sune manyan linzaman da suka zame mana masifu a wannan zamanin bakwai tarbiyyar bace kawai ta suɓuce mana. Da an taɓamu muce zamani, babu babban zamani sama da harsunanmu. Iyayenmu na baya da wahala kaga majalisar aibanta ɗiyan mutane, da wahala kaga wani ya zauna zinɗen yara marasa ji, idan yaga yaro yayi ba daidaiba zai hukuntashi batare da sanin iyayensa ba koya tsawatar masa ko ya masa nasiha. Amma a wannan ƙarnin sai dai mu koma gefe muna dariya ko yin ALLAH wadarai akan abinda munada damar gyarawa ko ambaton shiriyar ALLAH wa wannan yaron kuma tai tasiri garesa. Wani kuma zakaga a gefe sana’arsa itace saida kayan laifi ko wani mummunan abu dake ɓata tarbiyyar yara, shiyyasa sai UBANGIJI ya dawo da mummunan aikinsa wa zuri’ar tasa danta zame masa izina idan zai gane. Abinda kayi na yarda da auren yarinyar nan da ƙudurta gyara mata rayuwa batare da ƙyamata ba da ace haka muka dageyi a cikin al’ummar mu da an samu sauƙin yawaitar lalacewar yaranmu matuƙa. Domin duk wanda ya taimaki wani domin tsamosa daga wata halakar rayuwar duniya data lahira, shima UBANGIJI zai tsamesa da ga wasu masifu ya kuma tsame zuri’arsa ta inda bai zato ko tsammani ba. ALLAH yay maka albarka, ya ƙara mana yawaitar irinku acikin al’ummar mu. Dan irin waɗan nan yaran jawosu a jiki da haƙuri da yanayinsu ya dace muyi mu kuma maida hankali wajen fuskantar minene matsalolinsu. Kaifa abinda kake kallo ba dalili ba, wani a wajensa gagarumin dalilaine da zai iya tarwatsa masa rayuwa. In sha ALLAHU zakai nasara, wataran ba al’umma ba kai kanka sai kayi alfahari da jihadin da kayi da kuma kasancewarta iyalinka. Abu na farko da zakayi shine janta a jiki, karka ƙyamaci halin da take ciki, ka fuskanceta da ƙyau wajen gano minene ainahin abinda ya jefa rayuwarta a wannan yanayin dan na tabbata tanada ƙyawawan halaye itama da fuskantar ta ne zai bayyanar da su, sannan ka dage da addu’a, yin sadaka da ƙyautata mata, ka fuskanci abinda tafi so ka dinga jan ra’ayinta ga shi. Sai kuma ka ɗan dinga yin zafi kaɗan a wasu al’amuran dan irinsu zaka samesu da taurin zuciya da ƙin gane al’amura da wuri, dole idan ka hura wataran sai ka tauna, dan sai ka ɗauki matsayin miji ne wataran, wataran uba, wataran yaya, wataran abokin, wataran ƙani, wataran ma ɗa, haka zaka dinga canja mata kamar hawainiya dan yanda mata kance maza kamar yarane yanda ka renesu haka suke kasancewa, itama mace kamar gold ce, idan ka iya zama da ita ta yanda kaso kake sarrafata da adon da kake buƙata a idon duk wanda zai kalleta. Na ƙarshe shine haƙuri, dole sai kayi matuƙar haƙuri da zama mai juriya, dan wani lokacin zakaga kana tufkane kamar tana warwarewa, kada ka damu sai a hankali ɗabi’ar zata barta dan ta riga ta shigeta sosai ta yanda wannan abunne kawai ke sakata farin ciki da ƙarfafa ta saboda shi take kallo a matsayin dai-dai tunda a haka ta tashi taga kanta. Dolene kasa ido sosai a dukkan motsinta, ma’ana ka zama mai ankarewa akan ƙawayenta da abokan huɗɗarta danka janyeta daga irinta a cikinsu. Sannan fa saika shirya kawo mata wani abu mai ƙyau da idan kana yaƙin rabata da wancan ya zam kana cusa mata wannan, kasan kuskuren da mutanenmu keyi shine, kaita yaƙin cirema mutum halayen gurɓatattu amma baka bashi madadin abinda zai maye gurbinsa da shi ba, tayaya kake tunanin bazai koma ruwa ba. Sai kuma fahimtar da ita addininta, shine babban abinda zai iya tankwara maka ita cikin sauƙi ma fiye da komai. ALLAH yay riƙo da hannayenka kai da ire-iren ka game da irin wannan sadaukarwar. ALLAH ya sakakanka muku da sakamakon alkairi ku da zuri’arku a duniya da lahira da duk ma wanda zai iya koda tausasa harshene akan kuskuren wani.”
“Amin malam nagode sosai ALLAH ya saka da alkairi ya ƙara tsahon rai mai albarka. In sha ALLAH zanyi aiki da shawarar ka dan naji daɗinsu na kuma sake samun hasken da nake buƙata.”
Murmushi malam ya sake yi yana tattaro littatafai daga cikin tarin wanda ke a ɗakin nasa. Sai da ya kammala ya juyi ga Smart. “Ga waɗan nan kaje da su ka fara koyar da ita, ina dai fatan kanada karatu mai zurfi game da addininka?”.
“Alhmdllh akwai gwargwadon iko, a yanzu haka ma kuma ban daina nan ilimi ba ina zuwa islamiyya Sheikh Aliyu Abdur-ra’uff Maina (MUTUM DA DUNIYARSA) kafin abubuwa su taɓarɓare ne na dakata gaskiya, amma in sha ALLAH ina kan shirye-shiryen komawa na cigaba”.
“Masha ALLAH kayi ƙyan kai kuwa, Ai Sheikh Aliyu Maina mutumin kirki kuma aminina ne sosai, kaga idan kunyi nisa ka fahimci ta fara tankwaruwa zaka iya sakata Islamiyyar da matansa ke jagoranta suma Malam Jiddah da Malam Maimunatu”.
“In sha ALLAHU zanyi hakan malam”.
Sun ɗan ƙara tattaunawa sannan Smart yay masa sallama ya fito saboda su Ahmad dake jiransa. Ya samu sunata hirarsu da ɗaliban malam, amma duk da haka saida ya basu haƙuri sannan suka wuce yana jin zuciyarsa sakayau ba kamar daren jiya zuwa safiyar yau da yake cikin damuwa ba akan lamarin Lulu. Sai kusan shida suka iso Sharaɗa, Smart ya fita ya buɗe musu gate suka shiga har ciki. Suna sauke kayanta da suka taho da shi ya zare jikinsa ya shiga ciki dan fara duba yanayin shigarta kafin su Ahmad ɗin su shiga……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣7️⃣
…….Da sallama ya shiga falon, tana kwance a 3sitter idanunta a lumshe tamkar mai barci, sanye take da doguwar riga mara nauyi milk color data bi jikinta ta fidda ainahin surarta, sai dai bawai ta matseta bane ba, kanta babu ɗan kwali sai gashin data ɗaure a tsakkiya. Buɗe ƙofar da jin shiru kuma ya sata jiyowa tana buɗe luluu idanunta a kansa. Numfashi ya sauke a hankali da ɗan janye idanunsa batare da yace mata komai ba ya wuce ta, itama baki ta taɓe tare da maida idanunta ta lumshe. Minti kamar biyu sai gashi ya dawo riƙe da Hijjab a hannu, cikin motsa lips ɗinsa kaɗan kamar bayaso ya furta, “Ina tare da su Ahmad tashi kisa hijjab”.
Idanunta ta buɗe fuskarta a tsuke matuƙa da damuwar kaɗaicin da take ciki ita kaɗai a gida ba waya ba wani abin ɗebe kewa dan ba’a haɗa musu ba, kamar zata ɗauke kai sai kuma ta sake yamutse fuska cikin izzar nan tata ta furta, “Dan kawai kana tare da wasu sai na kama saka hijjab. Wai mi kake nufi da ni ne? Ko dan kaga na saka a waccan ranar kake tunanin cigaba da jin kanka sama can”.
“Mawaddat Umarni ne tashi ki saka hijjab ko nayi abinda bazai mana daɗi ba mu duka”. Ya faɗa shima cikin deep voice ɗinsa da dakewa yana tsatstsareta da idanun da take kira na macizai babu alamar wasa tattare da shi. Kanta ta ɗauke gefe a gatsine ta ce, “To yi ɗin mana”.
“Okay haka kikafi buƙata?”. Ya faɗa shima a dakensa yana ƙoƙarin kai hannu kanta. Tashi tai zaune tana watsa masa harara, dan babu abinda yazo a zuciyarta sai abinda ya faru tsakaninsu ɗazun, ita kuma abinda bazata iya ɗaukaba kenan taɓa mata jiki balle har yay tunanin sake maimaita abinda yay matan.
“Au ashe tsiwar taki iya baki ne? Da ki ƙi tashi ɗin mana kiga yanda zan tabbatar miki kan nawa a saman yake.” ya ƙarasa maganar yana jefa mata hijjab ɗin a jikinta ya juya ya fice. Wani irin kallon takaici ya riƙe maka maƙoshin nan ta bisa da shi, a zuciyarta tana ayyana (Mi wannan mutumin ke nufi da ni ne wai shin? Ƙoƙarin takani ko mi? Yimin gadara da nuna zafin kai ko mi? Humm aiko gidan ya tarar in dai nice, zan bashi mamaki a gidan nan mu zuba) ta yunƙura da nufin barin falon batare da saka hijjab ɗin ba. Sai dai tana miƙewar su Ahmad nayin sallama, ƙofar ta zubama ido kawai tama rasa miya kamata tayi har Smart ya shigo a farko, ja yay ya tsaya murmushin fuskarsa na ɓacewa ɓat, sai kuma ya rumtse ido da masifar ƙarfi zuciyarsa na dokawa da sauri-sauri, dan da gaske fa yanada kishi mai zafi, bai fahimci hakan ba kuwa sai a yanzu ɗin nan dan idanunsa har ji yake suna masa wani yaji-yaji. Koda ya buɗesu a kanta ita kanta sai da taji razani ya shigeta, dan cikin ƙanƙanin lokaci sun yi wani irin kaɗawa da canja launi, baice komai ba ya tako inda taken tsaye ya duƙa ya ɗauka hijjab ɗin ya warware ya saka mata. Su dai su Ahmad da sun riga da sun shigo basarwa sukayi, sai kuma ita Lulu a wautarta ganin ran Smart ya ɓaci sai tai niyyar sake ƙular da shi. Sai da ta saci kallonsa ta gefen ido sannan ta juya gasu Ahmad tana sakin wani sassanyan murmushi da faɗin, “Sannunku da zuwa, ni ai da har zan fara fushi”. Ahmad bai kawo komai a ransa ba tunda dama sun san juna da jimawa sai dai bawani mu’amala ke tsakaninsu ba mai ƙarfi dan Lulu fa ita da maza zira’i maitan ne. Shima murmushi yayi yana kaiwa zaune da faɗin, “Yauwa amarya. Ya kuke ya gajiyar biki? Duk da dai naga angon naki shi tun ɗazun”. Sai da ta sake satar kallon Smart ta ga yanda yay kicin-kicin da fuska ya kuma ƙi zama sai ta sake sakin murmushin da bama Ahmad amsa da “Gajiya kam tabi jiki, kuma ya taku gajiyar? Ya su Uncle Hameed”.
“Alhmdllh, Yaya kuma shima lafiya ƙalau yake”.
Kanta kawai ta jinjina, ta juya ga Faisal shima ta gaishesa sannan ta nufi kitchen tana dariya a ƙasan ranta. Ruwa da lemo ta ɗibo da kayan cin-cin, babu jimawa sai gata ta dawo ta ajiye gabansu. Yanzu kam Smart ya zauna, sai dai kansa a duƙe yana latsa waya. Komawa tai ta zauna itama tana ɗan murmushin santin da su Ahmad keyi na dubulan. Shi dai gogan kamar ruwa ya cinyesa a falon. Sai da ƙyar yay controlling kansa kodan Faisal dan ta Ahmad mai sauƙi ne zai iya fahimtarsa. Sai dai murmushin Lulu sukar masa zuciya yake kishi na sake riƙe masa maƙoshi. Haka dai ya danne har suka miƙe, kayayyakinta suka shigo mata da su sannan sukai mata sallama ita kuma ta basu kayan garar data juye musu a leda kowa da nasa ta ƙaro ma sannan ta zuba wanda za’a kaima Aunty Khadijah matar Abdull-Hameed (Coach) dan suna ɗasawa sosai itama kasancewar akwai ƙawance mai ƙarfi tsakaninta da Aunty Saliha. Suna fita ta koma ta zauna tana dariyar jin daɗin ƙular da Smart da tayi. Jinta take rai fess ita kam. A haka ya dawo ya sameta. Zama kawai yay baice mata komai ba dan a yanzu idan har yay magana ɓacin ransa ne zai bayyana a fili, dan haka yafi zaɓar zama shiru har zuciyarsa ta ɗan sassauta masa sannan ya tura mata ledar da wayoyinta ke ciki ya miƙe yabar wajen. Nanma da kallo ta bisa cikin taɓe baki kafin taja ledar ta buɗe. Sosai taji farin cikin ganin wayoyinta da laptop, cike da jin daɗi ta ɗauka tai bedroom domin saka caji dan duk sun mutu ba caji. Ga cajojin duk suna hanunta…..
Kiran sallar magrib ya fiddosa a ɗakinsa, ya ɗan zubama kayan da su Ahmad suka shigo da shi ido dan suna nan a inda suka ajiye, iska ya furzar batare da yace komai ba ya kwashe su ya fara shiga da su bedroom ɗin nata. Zaune take da laptop data jona a caji gabanta, tun ɗagowar farko da tai suka haɗa ido ta maida bata sake ɗagowa ba har ya kammala shigowa da kayan. Babu alamar wasa tattare da shi ya ce, “Bakiji an kira salla bane?”.
Tsayawa tai da ga danna laptop ɗin sai dai bata ɗago ta kallesa ba. Amma ta tsuke fuska alamar jira take yace kule tace cass. Takowa yay gabanta a hankali ya rufe laptop ɗin ya tura gefe. Dole ta ɗago yanzun kam ta dubesa da iyakar duk wani ƙarfi dan nuna masa yana shiga mata hanci fa. Kallon tsakkiyar ido sukema juna kowa da abinda zuciyarsa ke ayyana masa, dan ta gagara faɗar abinda tai niyyar da farko. Ita ta fara janyewa cikin taɓe baki. Sai kuma ta miƙe batare data tanka masa ba ta nufi toilet. Bayanta yabi dan yanzun ma yana son tai al’ala a gabansa kamar ɗazun, kasancewar shi yana da ita sai ya tsaya yana kallonta, ajiyar zuciya ya sauke a hankali ganin tayi kamar yanda ya nuna matan ɗazun, sai yaji kuma nauyin da zuciyarsa yayi ya ragu, dan har cikin ransa yaji ta burgesa, in dai har haka take da saurin fahimta da ɗaukar abu komai zai zo da sauƙi kenan, kafin dai tayin ne yake ganin zasu dinga kai ruwa rana.
A karan farko ya ja musu jam’i yau, abi mafi sakata sake nutsuwa a wannan jam’i yanda Smart ke raira karatun Alkur’ani a nutse da fitar sauti nagartacce. Bayan sun idar cikin fuskewa tai yunƙurin miƙewa domin bar masa wajen amma sai ya hana hakan ta hanyar riƙo mata hannu. Hannun ta kalla sannan ta ɗago fararen idanunta ta zuba masa. Shima ɗin dai ita yake kallo dan haka suka zubama juna ido kowanne najin idon ɗan uwansa na ratsashi har tsakkiyar ruhinsa. Da ƙyar Smart ya iya aro jarumta da ga cikin ɗunbin ƙwarin gwiwar sa cikin fitar sauti ƙasa-ƙasa ya furta, “Inada kishi! Inada kishi mai zafi! Inada kishi mai tsanani Mawaddat. Wannan gaskiya ce da nake gaya miki ita danki haddace a cikin muhimman abubuwanki ki kuma kiyaye saboda gudun randa zaki iya tabbatar da ainahina akan wannan kalmar. Komai zan iya ɗauka, idan nace komai ina nufin komai amma banda kasa riƙe kanki ko killace kanki ga wanina koda kuwa uwa ɗaya uba ɗaya suka haifemu da shi. Ki cigaba da sanin *_SMART_* kawai, idan kika ce *_ALIYU HYDAR_* ki ke son gani a zahirance, to fa tabbas wasan zai iya canjawa da ga duk yanda kike iya tunanin ko kwallonsa a tsarin zuciyarki. Duk abinda kikaji nace bana so to da gaske bana sonsa, idan kuma bana son abu bana iya dogon kawaici a kansa game da ɗaukar hukunci mai tsauri. Idan har kina son cigaba da gudanar da duk abinda kika fara da ga gidanku cikin salama to ki kiyaye….”
Rikitaccen abinda ta hango a tsakkiyar idanunsa mai kama da guguwar hayaƙin turnuƙun yaƙi ya sata kasa iya maida murtani. Ba wai ta fahimci ainahin curarrun kalamansa bane ba a yanda shi yake son ta fahimta ɗin, a salon da yay maganar ne kawai ke son tilasta fassara mata su. Ba’a komai take garaje ba musamman maida murtani, dan haka ta shanye kamar komai bai mata zafi ba dan tana buƙatar fashin baƙi kafin ta maida raddi, dan haka kanta tsaye batare data janye idanunta da ga cikin nasa ba duk da hakan na cutar da ita ta ce, “Ka gama?”…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣8️⃣
……Ba ita kaɗai ba, hatta shi ma kallon da sukema junan na ƙarshen ƙwal uwar daka na matuƙar zafafa masa garkuwar jiki, amma ya zaɓi nuna jarumtar nan da duk aka san Aliyu Zakin fama da ita ta taurin zuciya da tsaurin shanyewa ya ƙi janyewa. “Gamawata na nufin karɓar umarni na, saɓanin hakan kuma.. hummmm!” yaƙi ƙarasawa sai danne lips ɗinsa da yay da haƙori cikin tabbatar da gargaɗi. Itama saita danne natan da salon muzuba mu gani tana mai ɗaura ɗayan hanunta saman nasa da ke akan natan ta turesa masa. Komai baice mata ba, sai lumshe idanun nasa yay kawai. Saman gadon ta koma ta zauna tare da ɗaukar laptop ɗinta ta cigaba da abinda take yi batare data sake ko satar kallon inda yake ba. Sai dai zuciyarta taƙi samun nutsuwa dan kalamansa ne ke faman mata kai da kawo. Ba wannan ne karo na farko daya mata irin waɗan nan kalaman a cirkuɗe ba, na baya ma kuma sun cimata rai da zafafa ta harta ƙagautu da son jin fasararsu, amma na yau sai batajin suna mata raɗaɗi ƙagautuwar ce kawai ke zaburar da zuciyarta akan hasashen mai iya fassara mata su. Karan farko da taji tana ɗan kewar Nadiya, amma kuma hakan bazai sa tai kiranta ba. Duk da kuwa ta turo mata tarin sakwanni na ban haƙuri amma tai biris, hatta taron bikin nan Nadiya tata roƙon son zuwa, anan ne ta mata reply da cewar (ba’a buƙatar ki) da ga haka kuma bata sake bi takanta ba. Su Afrah kam bata ganin sunada hankalin da zata iya sakasu a sabgarta. (Mubeen ko su Hussain) zuciyarta ta ayyana mata. Mubeen ai ƙaninta ne, ita kuma bata son raini gara ma su twins ɗin, gamsuwa da hakan ya sata ɗaukar wayarta ta shiga WhatsApp, abinda bai dameta ba sai abu mai muhimmanci ya taso mata. Dubawa tai dan ganin wanene online, sai taci sa’ar ganin Hassan dan haka tai masa sallama sannan ta rubuta masa kalaman da Smart ya faɗa mata, (dan Lulu fa irin mutanen nan ne masu ƙwanya matuƙa, tanada saurin ɗaukar abu da haddacesa, ko’a makaranta ƙuruwace ta gaske da kaifin brain yasa zama popular ga malamai da ɗalibai, dan ma abubuwa da yawa sun faru da suka so taɓa mata karatun musamman ma harkar shaye-shaye ALLAH dai ne ya ƙaddara da rabon zata haye da amsa suna lawyer a yanzun). Sai dai anyi rashin sa’a tana turawa Hassan na komawa upline, sai kawai ta ajiye wayar da tunanin bari ta bashi mintuna tasan zai dawo, idan ma bai dawo ba zatai kiransa. Ta cigaba da aikinta sama-sama har akai kiran isha’i, har lokacin kuma Smart na’a ɗakin yana karatu ne shiyyasa shima hankalinsa ba’a kanta yake ba har sai da akai kiran sallar sannan. Yanzu ma koda yace tazo suyi jam’i bata musa masa ba, bayan sun idar ne ya dakatar da ita daga yunƙurin tashi ta hanyar tura mata littatafan da malam Nasirudden ya bashi. Littatafan ta zubama idanu, kafin ta ɗago ta kallesa fuska a tsuke.
Kafin ma tace komai ya bata amsa da “Naki ne, zamu fara karatu sai ki shirya. Dan ya kamata kisan addininki. Hakan ne zai sake tabbatar miki da ke wacece, ki kuma san yanda zaki bautaba UBANGIJI, ki yima mahaifiyarki da ƙasa ta rufema idanu addu’a, ta haka ne kawai zatai alfahari da ke dajin farin cikin barin baya da tayi, zaki san yanda zaki roƙa UBANGIJI da miƙa masa kukanki akan bukatunki ya amsa miki”.
Yana gama faɗa ya miƙe batare da jiran cewarta ba. Tayi niyyar maida raddi akan maganar farko, sai dai ta ƙarshe tai mata takunkumi da hakan, tana son mahaifiyarta matuƙa, tana tsananin begenta kuma. Duk abinda zaka jingina mata da ita yana saurin sanyayata koda batai niyya ba tayi, balle ma ita in dai akan neman abinda duk za’ace ilimi ne da zai amfaneta bataga dalilin dazai hanata amsa ba, a ganinta hakan ribarta ce, ta ƙara koyon abinda bata sani ba….
*_WASHE GARI_* kamar jiya kowa a ɗakinsa ya kwana, garama shi yaɗan leƙata kusan ƙarfe uku na dare daya idar da sallar daya tashi yayi. Samun ɗakin a buɗe ya bashi damar shiga, sai ya sameta tana barcinta a cikin lallausan duvet ɗin gadon, ta rage hasken tabar mai pink. Wayoyinta ya ɗiba duka biyu ya fita da su, kusan akansu ya ƙarasa daren sai gabannin asuba ya kwanta, ana kiran salla kuma ya tashi. Yau ma ya tadata yin sallar, sai dai yana fita ta koma tai kwanciyarta har sai da ya dawo yay mata jan ido sannan ta tashi. A lokacinne ya ajiye mata wayoyinta ya koma can ɗakin ya kwanta sai barci…..
Kusan takwas da wasu mintuna ta kammala shirinta tsaf, tayi matuƙar ƙyau cikin skert da riga na atamfa da suka fiddata tsaf, kamar kullum babu kwalliya, ɗan kwali ma bata ɗaura ba dan bata iya zaman wahalar ɗaure-ɗauren nan dama a gida Afrah ke mata. Sosai ta baza ƙamshi aka toshe ido da glass bayan ta yana ƙaramin veil a kanta ta naɗesa a kafaɗunta. Dan ƙyau kam tayi ƙyau kamar ka saceta ka gudu. Cikin takun nan nata na yanga da gayu ta fito ɗauke da tarkacenta, sai key ɗin motarta da aka kawota da ita kaɗaice a nan ɗin sauran ba’a kawo mata ba. Kanta tsaye ta doshi hanyar fita, sai dai me tana taɓa ƙofar ta jita a rufe. Ƙaramin tsaki taja da duban agogon dake a tsintsiyar hanunta. Sam bata son makara, dan haka ta nufi kitchen da nufi fita ta ƙofar baya, sai dai nan ɗin ma ɓam. Cikin ɗan jin takaici ta rumtse idonta da komawa falon, kayan hanunta ta zube a saman kujera ta nufi ɗakin Smart. Yana tsaka da barcinsa ya ji ana bubbuga masa gefen filon daya tada kai, da ƙyar ya buɗe idanunsa da ke jingim da nauyin barci ya sauke a kanta. Kauda natan tayi da ga kansa a gadarance ta ce, “Malam bani key zan wuce. Ka wani bi ka rurrufe ƙofofi kamar a prison”.
Kallonta yake shi dai da ga sama har ƙasa har takai ƙarshen maganarta. Ƙoƙarin tashi yay zaune ya jingina da gadon ya harɗe hannayensa a ƙirji rabin ƙafafunsa zuwa ƙugu lulluɓe cikin bargo.”
“Malam ka tsaya kana kallona kamar wata hoto, bayan kuma kaji na faɗa maka bana son na makara ko? Inada important abubuwa a office”.
Wani ɗan jan idanunsa yay kamar zai lumshe sai dai kafin ya rufe ɗin ya sake buɗesu a kanta. Cikin yanayin muryar wanda barci bai isa ba da ɗan taɓe fuska ya ce, “Ban fahimceki ba, sake maimaitawa”.
Kallon takaici ta watsa masa. Dan ta fara hasala. Amma sai ta danne da ƙyar a ɗan zafafen dai ta ce, “Wai kai miyasa komai a wajenka abin wasa ne. Kasan ko mi kake yi? Ka bani key ni ba neman jidali nake ba”.
“Humm ke idan ance miki ki fita a yau a kuma haka yanda kiken nan sai ki fitan?”.
Harara ta watsa masa cikin gatsali da faɗin, “Sai ka hanani fitar idan na tashi”.
“Okay haka kika ce? To ko zan tabbatar miki ko ƙofar gate bazaki fita ba, idan kema kin shiga duniyar mafarkinne sai ki farka, dan idan har kinga kin fita a gidan nan da sunan aiki sai next week ma. Sannan bada wannan shigar ba idan har kina son aikin naki kenan. Dan bazan hanaki yi ba saboda wasu dalilai na, amma ba’a yanda ranki ya raya miki ba. Yanzu a ƙarƙashin ikon Aliyu Mika’il Idris Mawashi kike ba su Daddy ba. Abinda ya tsara a gidansa dole shi za’ayi ko ana so ko ba’a so. Garama ki nufi kitchen haɗa mana break fast”. Da ga haka ya juya yay kwanciyarsa. Wani irin ƙarajin kiran sunansa ta ƙwala a matuƙar zafafe. Sai kawai yaja filo ya ɗaurama kansa ya toshe kunnuwansa ma ya maida idanunsa ya lumshe. Masifa ta fara zazzaga masa zuciyarta na raɗaɗi kamar zata fito ta baki, amma bawan ALLAHn nan yay biris da ita, da ya ga ma filon bazai masa ba sai ya ɗauki bluetooth ɗin sa da ke a bed side drawer ya manna a kunne ya saka ƙira’a abinsa. Fita tayi a ɗakin dan ta fahimci sai ta haɗashi da Daddy. Wayarta ta cira a handbag ta shiga dannama Daddy kira. Bugu biyu kuwa ya ɗaga dan fitowarsa a wanka kenan shima zai yi shirin office. Kafin ma yace wani abu ta sakar masa kuka da faɗin, “Daddy kaga mutumin nan ko? ALLAH ina raga masa ne saboda abinda Baba da Uncle You suka cemin, amma idan ya ce muyi ta inda ya ɓullo zan hargitsa masa rayuwa, nifa babu lallai babu dole zan dawo gida Daddy, garama komi Baban zaiyi yayi….”
Duk da abinda Daddy keji na yunƙuro masa shima sai ya danne da ƙyar, cikin tausasa harshe ya ce, “Baby kinga relax mi yake faruwa? Mi yay miki?”.
“Daddy Office fa zanje yabi ya kulle ƙofofin, naje ya bani key amma yay min banza yama saka bluetooth a kunne wai babu inda zanje sai next week, irin like kamar wata baiwarsa da ya saya a kasuwar bayi”.
Ƙololuwar ɓaci ran Daddy ya kai, a taƙaice ya ce “Ina zuwa”. Ya yanke kiran, number Smart ya lalubo a karo na farko ya danna masa kira. Kasancewar bluetooth a kunnensa ya sashi jin shigowar kiran a bazata, hannu ya kai ya zare guda ɗaya yana kai hannu kan wayar tasa ya ɗauka dan ganin wanene mai kiransa haka. Bai san number ɗin ba, dan baida Number Daddy, kamar zai share sai kuma dai ya ɗaga gudun kar yay mistake.
“To sannu isashshe”.
Kalmar data fara dukan kunnensa kenan a maimakon sallama………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣9️⃣
……..Cikin sa’a kuma ya gane muryar Daddy. Amma sai ya danne bai nuna ba, cikin dai nutsuwarsa ya ce, “Assalamu alaikum”.
“Da sallamar nake da buƙata da ita zan maka ai. Miye dalilinka na hana Mawaddat fita office ka kuma kulleta?”.
Shiru Smart yayi kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya furzar da numfashi kaɗan yana gyara kwanciyarsa. Sake tausasa muryarsa yay fiye da ɗazun ya ce, “Kayi haƙuri Daddy sallama wajibi ne ga musulmi, haka ma amsata ga wanda akaimawa. Kai ya kamata ka tunatar da ni hakan a matsayinka na mahaifi. Dan haka kayi haƙuri ka amsa min sallamata kafin muyi maganar da kake son. Assalamu’alaikum!”.
A cinkushe Daddyn ya amsa masa, Smart ya ɗan girgiza kansa sannan ya tashi zaune sosai. Cikin sake tsantsan da kai na girmamawa ya ce, “Daddy ina kwana”. Bai amsa masa ba nan kam. Shima sai bai damuba ya ɗora da faɗin, “Zan sake baka haƙuri a karo na biyu Daddy, dan ALLAH karka saka baki a wannan zancen dan a yanzu Mawaddat tana ƙarƙashin na ne. Inada damar zartar mata da hukunci akan abinda ya dace da kuma banbance mata wanda bai dace ba. Kai mana fatan alkairi kawai shi mukafi buƙata da sanya albarkar ku, na riga na gama yanke hukunci akan hakan babu kuma tunanin canjawa a tattare dani amin afuwa. Na Barka lafiya”. Daga haka ya yanke wayar tare da kasheta gaba ɗaya ya koma yay kwanciyarsa ransa fal mamakin halin surukin nasa.
Ƙaramin hauka ne ya kusan samun Daddy da ga can jin Smart ya yanke wayar bayan ya gama datsa masa zafafan magana kamar yanda zuciyarsa ta fassara masa. Ƙoƙarin sake kira yayi amma sai wayar switch up. Kaɗan ya rage ya maka wayar da ƙasa. Amma sai ya fasa ya maida akalar kiran kan Uncle Yousuf. Suna zaune shi da yara da akaima shirin makaranta suna breakfast kiran Daddyn ya samesa. Bai kawo komai a ransa ba ya ɗaga, sai dai kiran sunansa da Daddy yay a tsawace ya sashi rumtse idonsa. Sai kuma ya miƙe yabar daining ɗin ya nufi bedroom ɗinsa. Cikin tausasawa ya ce, “Yaya lafiya dai kuwa?”.
“Yousuf yanzun nan ka kira ɗan iskan yaron can ka faɗa masa ya sakar min yarinya tunda ba ubansa ya haifa min ita ba, har ni yake da bakin gayama Mawaddat ta koma ƙarƙashin ikonsa ya kuma yanke hukunci a kanta bazai canja ba kamar shine ya haifa min ita.”
“Ya Salam. Yaya Please calm down dan ALLAH muyi magana mana. Wlhy sam ban fahimci mi kake son faɗa min ba. Mi Aliyun yay maka ne?”.
“Miye ma bai mun ba, babu abinda ya manta na rashin kunya bai faɗa min ba. Shiyyasa tun farko na faɗa maka yaron nan ɗan zafin kai ne zai iya bamu matsa ta duk inda bamuyi zato ba. To gashi ya fara, ya kulle gida ya hanata fita aiki, ta masa magana ya ce sai next week babu inda zataje, ta kirani nai kiransa nai masa magana amma ya daddatsamin magana son ransa tsabar shi ya cika cikakken ɗan iska.”
Girgiza kai Uncle Yousuf yayi, kafin ya ce, “Dan ALLAH kayi haƙuri ka kwantar da hankalinka, ka dai san mi ɓacin rai ke haifar maka a yanzu. Zan kira shi na masa magana sai naji dalilinsa. Sai dai ma yaya banda abunka ai bai kamata ka biye mata kai kiransa ba, karfa ka manta yau kwana biyu kawai da tarewarsu, ai bai dace ba ta fita aiki sai mutane suyi magana kadai san yanda al’amarin yake yanzu mutane sun bar damuwa da al’amarin su sun koma hango na wasu”.
“Yousuf bana buƙatar jin komai, sannan ni babu ruwana da wasu mutane ko abinda zasu faɗa, farin cikin yarinyata kawai na sani. Shi wanene da zai tauyeta bayan da aikinta ya ganta, sannan waya faɗa masa shi ɗin har ma yanada wani ƙarfin iko a hannunsa a kanta da zaima mutane wani gadara koda ace auren nasu mai muhimmanci ne. Wannan shine na guda tun farko amma ka kasa fahimtata, shiyyasa kuma nace ayi komai a rubuce amma nan ma ka wani kakkaresa gashi nan tun kan aje ko ina ya fara nuna halinsa, a haka kwanakin da kace ɗin zai cika yay abinda ake so? an faɗa masa akan ƴata zai nuna gargajiyancinsa ne”.
“Naji duk na ɗauka kayi haƙuri zanyi magana da shi yanzun.” daga haka Uncle Yousuf ya yanke wayar batare da ya jira cewar Daddy ɗin ba. Hannunsa ya kai ya dafe kansa, sai kuma ya girgiza a hankali ya ɗago yana murmushi mai sanyi. A fili ya furta, “Yaya yaya kenan, kai da gaske jiran cikar lokacin kake kenan? Humm aiki ya sameka. Aliyun dama shine ai dai-dai da kai game da lamarin Mawaddat duka kai da itan. Ashe babu daɗi lokacin da ka dakatar da Aunty Kareema fita aiki a dalilin Marigayiya, duk da hakan ya mata ciwo kuma ta haƙura iyakarta kuka ta share hawayenta, ashe ita daga sama ta faɗo? Kai gashi hana fitar kwanaki kawai da akai ma taka ɗiyar ya zafafaka har haka. ALLAH na gode maka da ka kaini da rai da lafiyar ganin irin wannan ranar, shiyyasa akace yanzu ma tun a duniya ake fara hisabi basai an mutu ba. Muje zuwa yanzu aka fara wasan ai. Mai ƙarfi sai yaci kofin”. Ya ƙara sakin murmushi. Ƙoƙarin kiran Smart yayi sai ya samu wayar switch up. Ya sake sakin murmushi da faɗin, “Kaga mazan ƙwarai”. Da ga haka ya miƙe ya fito abinsa. Ya samu yara har sun wuce, sai Aunty Saliha da ke zaune tana tsumayen fitowarsa dan ya sakata a ruɗani.
“Abban Ra’is lafiya dai ko?”.
Ajiyar zuciya ya saki yana kaiwa zaune, ta turo masa kunun data sake zuba masa dan wanda ya bari ya huce. Sai da yasha kusan sau uku sannan ya dubeta. “Yaushe zakuje gidan Mawaddat ɗinne?”.
“Sai zuwa anjima kaɗan dan muje mu dawo da wuri ko”.
“Inaga ku kuyi zamanku, su Hussain suje sukai mata, motocin ta kuma a barsu ba yanzu ba.”
“Amma wani abu ya faru ne?”.
“Zai dai faru Saliha…….” nan ya zayyane mata komai daya faru. Cikin damuwa ta ce, “Amma Yaya da bai kirashi ba ai. Dan Aliyun ya fishi gaskiya, yaza’ai amaryar da aka kai gidan miji shekaran jiya kuma a ganta a office yau dole zai iya zama abin magana. Inda waɗan nan ƙananun matsalolin zai dinga sawa iyaye na neman sakin ƴaƴansu ai da kowama ya zama babu aure kenan. Ni sai nake ganin kamar maganar Aunty Kareema zata iya zama gaskiya….”
“Hummm ku mata kullum tunaninku iri ɗaya ne, miyasa komai a rayuwa idan yazo mana a yanayin da ba haka muke tunanin ganinsa ba sai mu dinga ɗaukarsa asiri. Nasan asiri yana ɗaya daga cikin abinda al’ummar mu suke kallon babbar mafita ga al’amuransu a halin yanzu, sai dai bai kamata muna tsuke dukkanin zukatanmu waje guda ba akan kowanne bigire muyi masa kallon asirin. Amma dai bari nai miki wata tambaya, shin ku minene dalilinku na kallon al’amarin Yaya matsayin asiri?”.
Duk da maganganunsa na farko sun shigeta sai bata gaza wajen faɗa masa hujjojin da suke kallonba su. Ta ce, “Na yarda da zancenka nima, sai dai ka kalla wani abu Abban Ra’is. Kafin auren marigayiya kai da kanka ka bani labarin ba haka Yaya yake ba sam, sannan Yaya nada ilimin addini mai zurfi da yasan minene aure da ƙaddara. Amma kaga yanda idanunsa suke rufewa ta yanda idan wani aka faɗamawa da bai gani ba zai iya ma ƙaryatawa. Dolene muyi tunanin akwai sammu tattare da shi”.
Murmushi yay da cewa “Hummm! Saliha kenan. Duk ilimin mutum bakwa tunanin son zuciya zai iya sakashi ajiye ilimin gefe ya aikata abinda baida alaƙa dana masu ilimin. A al’amarin Yaya babu wani asiri, akwai ɓoyayyen al’amarin da yake ɓoyewa dai tun kafin auren Mawaddat ɗin, sai da ya auretanne ya fara fitowa, wanda tamkar ALLAH ya jarabcesa da sanya masa tsoron faruwar irinsa akan Mawaddat ne, ba komai ya kawo hakan ba kuma sai dan itace mafi soyuwa a ransa ko kuma ana masa barazana da ita, shiyyasa ma tun farko ya gagara yarda da kowa game da kula da al’amarin ta, a tunaninsa shi zai iya kareta akan komai, sai kuma akai rashin sa’a ƙaddarorinta ba’a fatar jiki suke ba ko mahallin zamanta balle yay tunanin kuɓutar da ita a yanda yaso da kuma ƙarfinsa da wayonsa. Dan haka kuma bar damuwa da al’amarin sa ana gab da zuwa gaɓar da zai fallasa kansa da kansa batare da ya sani ba. Yanzu Mawaddat itace mafi ƙololuwar abar tausayi, dan ina matuƙar jin tausayin rayuwar yarinyar a dalilin halin data tsinta kanta a ciki.”
Yanda ya ƙare maganar cikin matuƙar damuwa da ɓacin rai yasa Aunty Saliha tasowa ta dawo kusa da shi tare da dafa kafaɗarsa. “Kayi haƙuri Abban Ra’is, tabbas tausayin Mawaddat dolene ga duk wanda ya fahimci muhimmancin rayuwa. Sai dai namu addu’a ce a yanzu tsakaninmu da ita, mu kuma cigaba da bama Aliyu goyon baya akan abinda ya fara, dan a yau na sake gamsuwa da fahimtar hikimarka ta haɗa wannan auren. Inaga kuma lokaci yayi da shima zaka fara aiwatar da shirinka na taimakonsa da tun farko shine dalilin jawosa jikinka da kayi, dan namiji bazai yiwu ya rayu babu abinyi ba yakan ja masa ƙasƙanci tsakaninsa da mace, musamman irin Mawaddat da tunda ta tashi bata san minene babu ba”.
“Hakane kam, insha ALLAHU kuma a yanzu haka ina kan shirye-shirye ni da Hameed, dan kin san al’amarin nasa sai anbi ta bayan fage yazo a bazata tamkar yanda maganar auren nan tazo a bazata. Dan bayyanawa na nuna zaburar da mai ƙullin ne”.
“Tabbas hakane, ALLAH ya bada nasara yasa shima iyakar wahalar tasa ce tazo. Ku kuma da kuke ƙoƙarin ALLAH ya saka muku da alkairi ya hana bayanku kuka”.
“Amin ya rabbi. Bara na kirata idan naga da yiwuwar kuje ɗin to”.
“To ba damuwa”………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣0️⃣
…….Zaune take a falo dafe da kanta dake matuƙar sara mata saboda ɓacin rai, a yanda take jinta zata iya aikata komai akan mutumin nan, amma ta zauna tsumayen kiran Daddy ne da yace ta dakacesa, sai dai an shafe kusan mintuna ashirin kenan shiru, hannunta ta janye tare da kallon wayarta da idanunta da sukai wani irin jazur. Wayar ta ɗauke da tunanin sake kiran Daddy ɗin kiran Uncle Yousuf ya shigo mata. Wayar ta tsaya tana kallo kawai, sai da ta kusa tsinkewa ta iya ɗagawa ta kai kunne, sai dai tayi shiru dan in har tai magana kuka ma zai iya ƙwace mata. Ƙaramin murmushi Uncle Yousuf yay da ga can da bazata iya jiyo sautinsa ba, kafin cikin tausasa harshe ya ce, “My Daughter yau babu gaisuwa ne?”.
Nan ma shiru ta kasa magana. Tofa yasan an kai ƙololuwar ɓacin rai kenan, dan haka ya sake tausasa harshe cikin komawa serious ya ce, “Mawaddat miya faru? Ko baki da lafiya ne?”.
Hawayen da take riƙewa ne tun ɗazun suka kufce mata, da rawar murya irin ta mai kuka ta ce, “Papa bazan iya ba, bana son damuwa gida zan dawo. Wannan ba rayuwan da zan iya yi bane…”
“Kwantar da hankalinki sanarmin mike faruwa?” ya faɗa like bai san komai akai ba. Da ƙyar ta iya masa bayanin abinda ya farun kamar yanda Daddy ya sanar masa. Anan ɗin ma murmushi ya sake yi ɓoyayye. Kafin ya ce, “Mawaddat rayuwar aure haka take, a komai ita mace ƙarƙashin ikon mijinta ta ke, wajib ne kuma yimasa biyayya in har shima bai keta dokar UBANGIJI ba ko jagorantar ta saɓa masa. Anan kam ba’a yarda ta masa biyayya ba sam, dan ba’ama wani biyayya ko tarayya wajen saɓama ALLAH……”
“Bazai yiwu ba Uncle You, domin ni da kai da shi duk mun san matsayin wannan zaman ba sunansa aure ba, Please Uncle kace masa ya sakeni idan ma bazai yi haka a yau ba zan dawo gida idan kwanakin da akai yarjejeniyar sun cika ya sakenin, zan iya ɗaukar komai amma banda kan aiki na, domin shine rayuwata, shine farin ciki na, shine mafarkina, shine babban burina tun kafin nasan kaina, shi waye da rana tsaka zai datse hakan da tunanin nuna gadara ko ƙarfin ikon abinda bashi da ikon!”.
“Mawaddat aure kona kwana ɗaya ne sunansa aure, da auren nan baida kimar da za’a kirasa ko kwallonsa da wannan martabar da muhimman mutane basu taru cikin shigar kamala domin ɗaurashi ba. Da wasu mutane basu ajiye muhimman ayyukansu ba domin halartarsa. Ki kwantar da hankalinki komai ya tafi cikin tsarin da muke fatansa, Aliyu kuma zanyi magana da shi duk da nasan shima ba son hanaki aikinki yake gaba ɗaya ba tunda ya sanar miki next week zakiyu resuming be a good girl mana sweetheart, maybe ma yana tsokanarki ne dan yaga yaya zakiyi. Dan haka ina son ki zama jaruma mana kamar yanda ya sanki…..”
“Amma Uncle fitan yanada muhimmanci fa yau. Kasan inada case ɗin yarinya da ke aibiti, tun juya kuma ya kamata naje na shigar da case ɗin court”.
“Kar ki damu indai wannan ne yanzu zan fita ni zanje da maman yarinyar mu shigar da ƙaran, ke kuma sai ki cigaba da shirinki matsayinki na lawyer ɗin nata hakan yay miki ko?”.
A hankali ta ce, “Eh”.
“Yauwa ɗiyar albarka na. Ki daure kinji, kar Aliyu ya samu na tsokanarki, bamma so ki bari yaga hawayen nan, maza ki sharesu ki zauna kurum kamar ba’ai komai ba Kinga kinyi winning”.
Ta gamsu da zancen nasa ɗari bisa ɗari, dan dolene itama ta mannama velleger ɗin can haukan da sai ya gagara barci a yau. Da ga haka ta miƙe bayan sunyi sallama da Uncle Yousuf da ke dariya daga can ta nufi bedroom. Fuskarta taje ta wanko da canja kayanta zuwa wando da riga marasa nauyi na zaman gida, ta sake dawowa falon ɗauke da laptop ɗinta. Dai-dai nan ya fito shima, alamunsa sun nuna yay wanka dan sanye yake cikin ƙananun kaya da sukai matuƙar amsarsa sai ƙamshinsa mai sanyi da ke tashi. Zaune ya kai idonsa a kanta sai dai fuskarsa babu walwala, duk da taji motsin nasa ko sau ɗaya bata nuna alamar hakan ba balle ta ɗago, lap-top ɗinta kawai take ƙoƙarin kunnawa. Shi kuma sai ya tsira mata idanun nan nasa na macizai da take kira, ƙin ɗagowar tata bai hanata jin kaifin idanun nasa a kanta ba, amma ta dake ta cigaba da abinda take yi.
“Break fast fa?”.
Ya faɗa a dake still dai idanun nasa a kanta. idan kujerar da ya ke zaune ta motsa to itama ta motsa. Cije lips ɗinsa yay yana wani sake ƙanƙance idanunsa a kanta. Kusan minti ɗaya yana kallon nata kafin ya miƙe tsam zuwa inda ta ke, lap-top ɗin ya ɗauke da ga jikinta ya ajiye gefe, karon farko ta ɗago ta kallesa da idanunta da suka kaɗa saboda kukan da tayi, fuskarta na nuna matuƙa ranta a ɓace. Nunawa yay kamar baiga kallon da take masan ba, kafin ta furta abinda ke bakin nata ya kwasheta gaba ɗayanta a cikin hannunsa yayi sama da ita kamar wata ƴar baby, (🤣dama abu ba abu ba sai masifa).
“Bana son wulaƙanci malam miye haka? Dalla sauke ni”. Ta faɗa cikin matsanancin ɓacin rai tana kai masa ƙananun duka a ƙirji, amma ko gezau kansa tsaye ya nufi hanyar kitchen da ita, saman cabinet ya direta, ya juya ya sakama ƙofar key. Dai-dai ita kuma tana dirowa da ga inda ya ɗauratan ta iso ga ƙofar. Wani shegen kallo ta watsa masa da faɗin, “Matsa min”.
“Idan kinyi abinda nace kenan”.
Ya faɗa cikin halin ko’in kula yana saka key ɗin cikin aljihun wandonsa da jingina da ƙofar yana mai harɗe ƙafafunsa waje guda. Ƙarshen ɓacin rai Lulu ta gama kaiwa, dan haka cikin kaushin murya ta ce, “Kasan na iya fiye da abinda kake tunanin ka’iya na rashin mutunci ko. Aliyu! Ka buɗe ƙofar nan ka bani hanya na wuce kafin na saka dana sanin sani na”.
Jikin ƙofar ya bari da ɗan taɓe baki batare da yace komai ba ya nufi frizzier ɗin da ke kitchen ɗin ya buɗe, sai da ya ƙarema kayan ciki kallo sannan ya rufe ya nufi store. Daga sama har ƙasa yake bin store ɗin da aka tsatstsage da kayan abinci kala da iri da kallo shima, har da su doya da airish da ruwa da kayan miya da akaima ajiya irin wadda bazasuyi saurin lalacewa ba. Shi sai abin ma ya so bashi mamaki da dariya, to su da suka jibge waɗan nan kayan matar gidan ta iya abinci ne?….
Shigowar Lulu a fusace ya saka tunaninsa yankewa, ya juyo gaba ɗayansa yana dubanta, huci take sosai idanunta sun juye gaba ɗaya har wani tara ƙwallan masifa sukeyi. Gashi yanda yaga sun ɗan kumburo tun ɗazun ya fahimci kuka tayi, yaji ba daɗi a ransa, dan sam baya son ganin wani ya shiga damuwa a dalilinsa, sai dai dolene yay abinda yayin dan ya fahimtar da ita da da yanzu ba ɗaya bane, yanzu komai sai da izini… Da sauri ya dubeta jin tana ƙoƙarin saka hannu a aljihunsa alamar son zaro key. Hannun nata ya riƙe yana ɗan waro idanu waje, duk yanda taso fisgewa bai sakar mata ba sai da ya zare key ɗin da ga aljihun nasa, sai kawai ya maƙalashi jikin belt ɗinsa ta inda yasan bazata ce zata ɗauka ɗin ba yana sakin wani shegen murmushin mugunta. Da sauri ta ɗauke kanta da ga dubansa gaba ɗaya tana jin kamar ta fasa ihu, a zuciyarta kuwa tace (ɗan iska).
“Yanzu mi zaki dafa mana? Dan yunwa nake ji nikam ga shi nace su Ammah kar su ƙara aiko abinci injiki.”
Harara ta watsa masa cikin gatsali ta ce, “Ashe zaka mutu da yunwa kuwa a gidan nan”.
“Zadai mu mutu, dan kema dai duk tsiya dole ki nema ai. A yanzu ma haka idan kina son fita da ga kitchen ɗin nan ki nema mana abinci, inba hakaba ALLAH anan zamu yini”. Ya ƙare maganar yana fitowa da ga store ɗin. Ɗaya da ga cikin kujeru huɗun da aka sakama table a tsakkiya yaja ya zauna. Hankalinsa kwance ya jawo wayar ya fara buga game ɗin ball, ya kuma ƙure ƙarar yanda ta cika kitchen ɗin da hayaniya. Lulu data gagara fitowa a store kanta ta dafe, sai faman haɗiyar rai take zuciyarta na ƙuna. Ta rasa yaushe ne guy ɗin nan yay mata irin wannan rainin har haka, bata taɓa haɗuwa da mutumin da ke latsata a yanda yake so da gadararsa irinsa ba, ya bala’i bala’in shigar mata hanci da yawa. Gadararsa da son nuna shi ɗin wani ne da iya taurin kai na cimata zuciya. Fitowa tai a bisa shawarar da zuciyarta ta bata, ta cije lips ɗinta tana jin kamar idan ta ƙarasa garesa ta shaƙesa kawai, amma sai ta ture tunanin gefe. Kujerar dake kallon wadda yake zaune ta dafa cikin ɗan sassauta zafinta dan ta fahimci ihun da take masan kamar tunzurashi yake da jin daɗin latsata. “Aliyu kafa san aiki nakeyi ka ɗakkoni ka kawo nan, kai miyasa baka bambance lokacin shiririta dana serious?”.
Batare da ya ɗago ya kalleta ba hankalinsa ma akan game ɗin sa ya ce, “Yima mijinki girki ne ba serious ba?”.
“Kai kasan mijin ma, Ka bani key na wuce, idan abincin kake so ai kasan gidan abinci, dan in har abinda zan girka zakaci ka siyama kanka wahala dan ban iya ba ma sai kabi wani sarkin”.
“Hummm ashe kuwa in dai ba zakiyi abinda nake so ba kuma ya dace ga matar aure to aikin ma zai gagareki yi ne, duk da a farko banda wannan niyyar. Dan haka kina da zaɓi kenan, yin yanda nake so kuma na tsara a gidana, ki samu yanda kike so kema. Ko ƙin yi, kema ki ƙi samu. Abinci kuma duk yanda kika iya kiyi zanci a hakan ko baiyi ba”.
Luuuu tai da idanunta kamar zata lumshe su sai kuma ta buɗe, komai ma ya gundireta, tama rasa yaya zatai da mutumin nan mai shegen taurin kai da gadara. Wai miyasa ma ta amince ne da wannan tsarin da shi? Miyasa bata bada damar a nema wani ba?. Tsaki taja mai ƙarfi da kai hannu ta dafe kanta, sai kuma ta janye tana mai watsa masa hararar zaka banbance tsakanin aya da tsakkuwa ta bar wajen. Da kallo ya ɗan bita ganin ta nufi hanyar store, tana shiga yay mata gwalo da sakin murmushi nan nasa da take kira na mugunta yana kashe ido ɗaya a hankali ya ce, “2-0 Madam”……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣1️⃣
……..Tana fitowa ɗauke da dankali ya fuske kamar bashi ba ya cigaba da game ɗin yana satar kallonta ta gefen ido. Ganin ta fara firar dankalin ya sashi ajiye wayar tasa a table ɗin ya miƙe, gefenta ya tsaya kaɗan, ya ɗauka wuƙar data ajiye saman chopped board ya fara yanka wanda ta fere, bata kulashi ba, ba kuma tayi magana ba ta cigaba da ferewa tana ajiye masa. Shima sai baiyi magana ba ya cigaba da yankawa, idan ya ɗan tara sai ya zuba a cikin ruwan data ajiye a bowl. A haka har suka kammala, kasancewar ta rigashi gamawa ita ta fara barin wajen ta ɗakko preyn fan ta dawo inda yaken ta zuba ruwan sabulu kaɗan ta wankesa da soso ta ɗaureye duk yana satar kallonta. Komawa tai gaban gas ta kunna ta ɗora sannan ta zuba man data ɗakko. Dai-dai nan ya kammala, sai ya wanke mata dankalin ya sake masa ruwa ya tace sannan ya juyo yana miƙa mata robar. Sai da ta hararesa ta amsa, shi dai ya gimtse dariyarsa da ƙyar ya juya yana ɗauraye wuƙa da sauran abinda sukai amfanin. Lulu kam koda albasanta ya soyu ta zuba dankalin sai ta nufi frizzier, kifi tai ƙoƙarin cira sai dai sanyin da ya ratsa mata hannu ya sata faɗin, “Ouchh!!”. Juyawa yay yana kallonta, ganin yanda take yarfe hannun ya sashi nufarta, hannun ya riƙo ya saka cikin nashi ya rumtse ɗumin nasan ya ratsata, sai kuma ya jawota gaban fanfo ya kunna ruwa ya ɗauraye mata hannun, sannan ya jawo ƙaramin towel ya saka mata hannun ciki. Komawa yay ya ciro kifin har biyu masu ɗan girma ya dawo ya wanke su sannan ya dubeta, ɗauke kanta tai da ga kallon gefen ido da take masa. Shiko da ba lura yay ba ya ce mata “Yankawa zakiyi?”.
Ƙaramar harara ta sakar masa da tura baki gaba sannan tace e.
“Kai dai Aliyu kana shan harara wlhy abin tausayi”. Ya faɗa yana yanka kifin. Hararar tasa ta sake yi da matsawa gaban dankalinta ta da ke cikin mai……
Kusan a tare sukai aikin, sai dai itace ke girkin shi kuma yana taimaka mata da yanka miƙo, duk da dai ba itace ke cewa yayi ɗin ba. Ya shiga matuƙar mamakin ganin yanda take girkin dama yanda tayisan, dan harga ALLAH bai kawo ta iya abinci ba. (Sai dai abinda Smart bai sani ba girki yana cikin hubby ɗin Lulu, tana son girki kuma ta iya kalolin girki na zamani sai dai fa sai ta gadamar yi take yin, tamafi sakin jiki tayi idan taje gidan Dada (kakarta matar Alhaji Garko) amma idan kaga tai girki a gidansu ko gidan Uncle Yousuf lallai ƴan arziƙinne a kanta ko taso yima Daddy wani bazata ko Uncle Yousuf ɗin). Abinda tai ɗin ya sashi jin daɗi bai ji ƙyashin tayata suka gyara kitchen ɗin ba duk da ma ba wani ya ɓaci bane dan Lulu akwai iya ƙwaf-ƙwaf ɗin aiki komai aka taɓa ana wankesa ne da zarar an gama da shi, inda ko ruwa ya taɓa za’a goge, tana hakanne kuma saboda yanayin tsaftarta, hakan kuma sai ya sake bama Smart nutsuwa kasancewarsa mutum mai shegen tsantseni da tsantsami. Dining takai komai ta ajiye tai wucewarta bedroom batare da ajiye plate ko kofin da za’ayi amfani ba. Baiyi magana ba saboda kiran Uncle Yousuf da ke shigo masa. Kiran ya amsa ya koma falo ya zauna. Har ya kammala wayar bata fito ba, dan haka ya miƙe yabi bayanta. Samunta yay kwance a kan gado rufda ciki sai dai ta canja kayan jikinta zuwa wasu, a hankali ya sauke ajiyar zuciya tare da yin gyaran murya. Kamar bazata kulashi ba sai kuma ta buɗe idanun kaɗan a kansa. Cikin ido suka kalla juna, ta janye nata da wani yin gaba da lips kamar mai son yin zinɗe, ta ce, “Wlhy in ma da wani abun kazo bazanyi ba na gaji”.
Dariya taso bashi dan yanda tai maganar da iyakar gaskiyarta, amma sai ya dake da ƙyar ya ce, “Ni na isa na sake saka Madam aiki ai tsaurin idon nawa ma sai yayi yawa. Sannu nazo yi miki, da kuma ban haƙiri da bikon kizo kici abinci. Har dama tausa idan kina so ƙyauya”.
Cikin taɓe baki da harararsa akan zancensa na ƙarshe ta ce, “Kai ne handin burum kaje kaita ci”.
“To Aliyu Hydar ka ƙara samun cigaba kenan, da ga illiterate velleger ka koma Maye, yau kuma handin burum, ɗan Ammah baban Ammah mijin Mawadda….”
Filon da take kwance ta fisga kafin ma ya kai ƙarshen sunanta da taji ya kamo ta wulla masa. Da sauri ya cafe yana zaro idanu, ya ce, “Madam ina rabaki da halin jifar nan kar wataran ki ɓazge min hanci kamar yanda Iffah tai ma Uwa fa tom”.
Wasu ta sake fisga tana tashi zaune ta cigaba da jefa masa su, tun yana karewa har ya fita yana dariya dan ya kula dai fushin ake saukewa a haka. Ƙwafa tayi itama da ballama ƙofar harara kamar itace tai mata laifin…..
Shi da kansa ya ɗebo plates ɗin da spoons bayan ya wanke su, ya zauna a ransa yana faɗin (Bari muci girkin ƴar madara muji). Da tea ya fara, lokacin da ya kai dankali da source ɗin ƙwai bakinsa sai da ya lumshe idanunsa. Wannan fa shi ake kira kama da wane bata wane, UBANGIJI mai rahama. UBANGIJI mai jin ƙai da baya haɗama bawa zafi biyu, idan ya jarabceka ta nan sai ya sauƙaƙa maka ta can dan kaji sanyi. A duk inda kaga mutum da halayya mara ƙyau kar ka yanke masa hukunci da ɗari bisa ɗari ɗin munanan ayyukansa, UBANGIJI shine kaɗai yasan abinda ke cikin zuciya da sirrikan ɓoye ga bayinsa. Ita dai a zahirinta duk wanda ya ganta suna ɗaya zai bata, amma a baɗininta sai UBANGIJIN da ya halicceta ya san kayarsa, sai ko wanda ya ƙaddara ya santan kamar dai shi mijinta a yanzun…
Yana gab da kammalawa ta fito, sai dai yitai kamar bata gansa ba ta zauna a falo ta ɗauka laptop ɗin ta ta cigaba da aikinta na ɗazun batare da kallon ko inda yake ba ko sau ɗaya. Shi ko dai sai satar kallonta yake time to time. Koda ya kammala sai ya ɗibo farfesun kifin cikin dauriya dan baya son kifi shi sam da tea ya nufota, ƙaramin coffee table ya jawo gabanta ya ajiye, ƙamshin kifin ne daya dakar mata hanci ya sata ɗagowa, harararsa tai ƙoƙarin yi yay saurin faɗin, “Ni dai tausaya min da hararar nan gidan ma zan bar miki karki lashe ni Ammah ko yaye ni batai ba”.
Hararar tasa dai tai ta ɗauke kai, sai kuma ta sake ɗagowa ta dubesa, karan farko ta saki murmushin da ke bayyana beauty point ɗinta da farare haƙoranta, ga wanda ya santa a kallo ɗaya zai fahimci na mugunta ne, saboda bata murmushi sai ta so, wanda kuma bai santa ba zai ɗauka yinsa matsayin birkita kwanyar duk wanda ya kalletan ne. Girarta a sama ta ce, “Waye zai fitan? Ka manta yau a gidan nan babu shiga babu fita? Ai duk yanda ka dama haka kowa zai sha wlhy. Ta miƙe ta nufi hanyar bedrooms. Da kallo kawai ya bita na mamakinta ne ko na son ƙarin bayani akan maganar tata ne oho masa. Yana a wajen harta da dawo da keys a hannu, a kallo ɗaya ya gane na ƙofar falon ne da ƙofar kitchen ta baya. Sai da takai zaune sannan ta tura su cikin rigarta a gaban idonsa ta gyara tana ɗaukar tea ɗin da ya ajiye mata ta kai baki.
“Idan ma wasa kike ki daina. Uncle Yousuf fa ke jirana tare da Yaya Abdull-Hameed”.
“Oh really?”.
Ta faɗa cike da rainin wayo. Hannu ya kai ya dafe kansa, sai kuma ya kai zaune a kusa da ita cikin lallashi ya ce. “Mawaddat Please seriously wlhy jirana akeyi, babu jimawar nan yay kirana kuma important ne zuwa 12”.
Batama ko kallesa ba balle ta tanka masa, sai ma kifinta data fara ci a hankali tana wani lumshe idanu taba banza ajiyarsa. Rasama mi zaiyi yay, cikin son ta fahimta yay ƙoƙarin kamo hanunta ta balla masa harara. “Karka kuskura hannunka ya kai jikina. Ka kuma kiyayi yin hakan inba haka ba kasha mamakin sanin ainahin Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi. Kasan bazaka iya ƙarasa wasan ba miyasa ka fara? Common ƙyaleni bana buƙatar hayaniya, ba kace da ni zaka buga game ba? Muje zuwa”.
(Tana mun magana kamar wata lady boss) ya faɗa a zuciyarsa. A zahiri kam kansa kawai ya dafe. Abu tamkar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa har 12 tayi Lulu bata da niyyar bama Smart key ɗin nan, zuciyarsa na raya masa ya turmuzeta ya amsa amma yana gargaɗin kansa karta tada masa aljanu, dan yasan mata da iya aljanu. Sha biyu da kusan kwata kiran Uncle Yousuf ya shigo masa. Ya ɗaga ya gaida shi da mutuntawa kamar yanda ya saba. Da ga can Uncle Yousuf ya ce, “Aliyu yaya dai? Kai muke jira na ga har 12:15?”.
Ɗan kallon Lulu da ke ta aikinta a laptop tana zuba murmushin mugunta yayi, a can ƙasan maƙoshi ya ce, “Uncle ta kwashe keys ɗin ne fa, wai tunda na hanata fita nima babu inda zanje”.
“What! Mawaddat ɗin? Kaga bata wayar Please bana son shiririta”
Maimakon bata sai ya saka a hansfree yanda zataji, kiran sunanta da Uncle Yousuf ɗin yay ya sata ɗagowa ta kalla wayar, sai kuma ta amsa da “Yes Papa good afternoon”.
“Afternoon Dear. Miya faru kika hana Aliyu fitowa ga shi munata jiransa?”. Murmushin muguntar da take ta faman yi tun ɗazun alamar duniya ta mata daɗi ta sake saki da faɗin, “Uncle You shi ya zaɓi hakan ai, dan haka ka manta da shi kawai, dan yanda ya hanani fita sai dai mu yini tare a gidan.”
“Mawaddat Please!!”
“Uncle please”.
Ta faɗa itama kamar yanda yayin tana tura baki. Kai kawai Uncle Yousuf ya dafe da ga can, yayinda Coach ke kwasar dariya dan Smart ɗin kawai ya ke hangowa, kai mace daban ce, yo inba mace daban take ba Smart ɗinsa ne da ya sani mai tsaurin nan da rashin son magana za’a kullema ƙofa a hanashi fita. Aure aunre yayi. A ɓangaren Uncle Yousuf kam iyakar lallaɓa yay ma Lulu tafa ce ba gudu babu ja da baya, har ya koma faɗa amma tai biris, ba komai ke tunzurata ba kuma sai ganin yanda fuskar Smart ta fara canjawa da dauriyar da yake zuwa ɓacin rai. “Uncle bye”. Ta ce cikin siririyar dariya tana miƙewa tare da laptop ɗinta da wayoyinta tabar falon ma tana ɗagawa Smart yatsu biyu na ƙularwa ta ce, “2-1 ka shirya yin game over gaba kaɗan”.
Wani irin bahagon iska ya furzar da ga bakinsa yana mai dafe kansa. Da ga can cikin tunzura shima Uncle Yousuf ya ce, “Aliyu wai yarinyar nan tafi ƙarfinka ne da karɓar key a wajenta ya gagareka. Be a man mana Son”.
“Uncle bazaka gane bane wlhy, yarinyar nan azababbiya ce, tafa saka key ɗinne…..”
Sai kuma yay shiru fahimtar ɓaranɓaramar da yake neman yi. Uncle Yousuf zai sake magana coach ya katsesa da faɗin, “Kaga ƙyaleta muje mu samesa a can kawai nikam, dan amarya dai bata laifi koda ta kashe ɗan masu gida. Zakina jiramu karka damu”.
Kafin Smart ya ce wani abu an yanke wayar, sai kawai ya girgiza kai. Wannan ma sauƙin kan na Coach ya sa yake sake jin ƙaunarsa a ransa. Mutumin nan shi na musamman ne a garesa, dan ya taka rawa kala-kala a cikin rayuwarsa da har abada bazai manta ba……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣2️⃣
………Cikin mintuna da basu wuce ashirin ba sai gasu sun iso, jin horn ɗin su da kiran da Coach yay masa ya ce gasu sun iso ya saka shi miƙewa ya nufi bedroom da ta shige. Fuskarsa babu walwala da ga bakin ƙofar ya tsaya yana kallonta da faɗin, “Sun iso Please ki kawo naje na buɗe musu”.
Ɗagowa tai ta ɗan hararesa da maida kanta tana taɓe baki, “Oh wai har yanzu kana tunanin amsa cikin sauƙi ko min wayo? To anƙi a bada ɗin na ƙarfi ne”.
Kaɗan ya cije lips ɗinsa da jin jina kai yana wani ɗan murmushi, dan ya fahimci sai yayi abinda tun ɗazun yake hana kansa yi sannan. Takowa yay zuwa gaban gadon tare da kaiwa zaune cikin lallashi ya ce, “Mawaddat su Uncle Yousuf ne fa, kuma na faɗa miki magana mai muhimmanci zamuyi….”
“Nima ai aiki da zan fita yi mai muhimmanci ne ka sani. Gara ma ka bar wani sauke murya ba badawa zanyi ba ehe”. Ta juya ta cigaba da aikinta.
Lips ɗinsa ya sake cijewa da faɗin, “Amma kin san zan iya amsar key ɗin a duk ta yanda naso ko?”.
A gatsine ta ce, “To ƙarɓi ɗin mana”.
“Haka kika ce?”.
Shiru ta masa kamar bata ji ba, sai ma faman murmushin ta take tana sarrafa system ɗin gabanta cike da ƙwarewa dan charting take yi da wata friend ɗinta ƴar ƙasar Hong kong da sukayi karatu a America tare. Laptop ɗin gaban nata ya janye gefe tare da birkitota, zabura tayi dan batai zaton zai yi yunƙurin amsar ba, sai dai kafin tayi wani yunƙuri ya danneta da rabin jikinsa ya riƙe hannayenta duk biyu a cikin nasa. Rawa jikin nata ya fara yi saboda yanayin na neman maimaita kansa ne da abinda ya shuɗe, amma cikin ƙoƙarin dakewa ta ballara masa harara. duk da shima ya fahimci hakan bai bi takanta ba sai ma baki da ya taɓe da sakin murmushin nan nasa data raɗa ma suna na rainin hankali cikin kashe ido ɗaya ya ce, “Zaki bayar da arziƙi kona ɗauka?”.
Sosai ta waro idamunta da suka cika da ɓacin rai ta ce, “Saboda kai ɗan is…..”
Baki ya taɓe da faɗin, “Oh ɗan iska ko?” sai ya ƙara ƙasa da murya yana kai bakinsa jikin kunnenta ya raɗa mata, “Dole ne ma nayi iskancin nan dan banzan amsa sunan nan a banza ba”.
“Aliyu!!”
Ta faɗa tana zaburowa gaba ɗayanta sai dai har ya riga ya tura hannunsa a rigarta ya ciro key ɗin. “3-1 Madam” ya faɗa yana sakin mata hannu da ɗagata murmushin mugunta fal fuskarsa ya nufi ƙofa ya fice harda mata gwalo.. Rumtse idanunta kawai tai da masifar ƙarfi tana ƙoƙarin dai-daita numfashinta dake rawa a maƙoshi……
Koda ya fito cikin girmamawa ya tarbi su Uncle Yousuf ɗin, basu shiga ciki ba kamar yanda ya buƙata, sai suka zauna a ƙarƙashin rumfar bunu da ke a harabar gidan domin hutawa. Ya gaishesu cikin mutuntawa, yayin da Coach ya tasashi a gaba da tsokana, murmushi kawai yake yi amma ya kasa cewa komai. Uncle Yousuf ya harari Coach da faɗin, “ALLAH kai dai anyi Yayan kwabo, ka ƙyale min yaro ya huta”.
Cikin dariya Coach ya ce, “Oh ashe fa kai yanzu ka tashi da ga Yaya ka koma suruki. No wander bakin Zaki na ya sake zama rumus yau. Bara to na tausaya masa sai ka matsa na ɗora da ga inda na tsaya dan ba barinsa zanyi ba fa”. Murmushi kawai Smart ke yi dan in dai Coach ne ya riga ya saba da wannan barkwancin nasa. Dama kuma can bai iya maidawa balle yanzu da yake ganin Uncle Yousuf da ya ƙara girma a idonsa na wajen. Sake gaisawa sukayi kafin su fara tattauna abinda ya tarasun. “Aliyu nasan ka ɗokantu da son jin dalilin wannan zama namu, kamar yanda muma muke a ɗokancen”.
“Haka ne Sir, dan da har na fara tunanin ko nayi wani laifi ne ma”.
Murmushi Uncle Yousuf da Coach sukayi a tare, kafin Coach ya cigaba da faɗin, “Aliyu kai na daban ne ai, duk da dai ɗan adam tara yake bai cika goma ba. Bakai laifin komai ba abinda muketa fatane da buri ya kasance. Yousuf abokina ne koma nace maka ɗan uwana dan ina jinsa tamkar matsayin twins brother, kamar yanda ka sani ya sanni da kai tun kana ƙaraminka, sannan masoyine naka dan yana ɗaya daga cikin wanda suka dinga goyon bayanka matuƙa, sannan ya taka rawar gani matuƙa a baya na son ganin ka ƙetare ƙasar nan amma ƙaddara ta hana hakan. Bai haƙura ba ya cigaba da shigi da fici na ganin abubuwa sun dai-dai har kawo yanzun nan bai huta ba. A yanzu dai a matakin ƙwallo shekarunka sunja Aliyu, sai dai Alhmdllh yanayin jikinka da kula da motsashi yasa kai tsaye baza’a iya cewa ka kai shekarun da kake ɗin ba a yanzu. Dan haka mataki na farko shine mun zabge maka shekaru a rubuce, mataki na biyu yanzu zaka daidaita cin abubuwan da duk suke saka jiki nauyi domin samun daidaito, sannan zaka sake jajircewa da training. Inata kai ka ban faɗa maka dalilin zancen ba. A karo na babu adadi Yousuf ya sake maidaka duniyar ƙwallon ƙafa a yanzu, a kuma matsayin manager ɗin ka. Duk wani abu da zamu iya kallo a matsala yayi iya bakin ƙoƙarin sa na shiga da fita wajen gyarashi da alkintashi cikin nasara kasancewar sa mutum mai kutsa-kutsa da huɗɗa da mutane a ƙasashen ƙetare. A yanzu haka ka samu team a ƙasar London in sha ALLAH signing da abinda baza’a rasa a kawai ya rage”.
Shiru kawai Smart yay yana saurarensu, har sai da Coach ya kai ayar bayaninsa sannan ya dubesa ya dubi Uncle Yousuf ɗin ƙwalla na cika masa ido. Kai Uncle Yousuf ya girgiza masa da masa alamar zip a baki baya son yace komai kenan. Wani irin al’amari mai girma Smart ya haɗiye tare da duƙar da kansa yay shiru ba tsawon mintina. Ba komai yake ba face kwararoma waɗan nan mutane biyu addu’oi kala da iri, sai da ya kammala sannan ya ɗago cikin ƴar damuwa. “Kun hana nace komai duk da inada abubuwan faɗa masu yawa. Ku na dabanne a garen….”
“Shiiii!!” Uncle Yousuf ya faɗa cikin dakatar da shi. Dole ya haɗiye tarin yabo da godiyar dake gumtse a zuciyarsa zuwa baki, ya tsira musu idanu kawai, sai kuma ya nisa a hankali “Amma Sir bakwa gudun a sake samun makamanciyar irin waccan matsalar?, bana son ku sake shiga matsala a dalilina”.
“In sha ALLAHU bama fatan hakan Aliyu. Kuma ai mu fatanmu wannan dabarar ta zama mafita. Ball hubby na ka ne, na sanka komai akace kayi ba ita ba zaka iya yin amma badan hakan na maka daɗi a rai ba. To a rayuwa duk abinda bawa zaiyi badan yana son abin nan ba zakaga yana tafiya ne babu wani armashi. A wannan karon bawai kai tsaye muke son ayi hakan ba, sai da muka duƙufa addu’a mu da su Ammah gaba ɗaya kafin ma duk wannan kai kawon na Yousuf, dan na tabbatar addu’oi nasu ne suka shiga kan gaban komai ya tafi mana yanda mukai fata ƴan matsalolin da suka faffaru ba wasu masu yawa bane gaskiya”.
“Su Ammah?!…”
Smart ya faɗa da ɗan mamaki, kai Coach ya gyaɗa masa da faɗin, “Yes da ga ita har Abba sun san komai akan wannan, kuma Alhmdllh bamu sha wahala wajen amincewar tasu ba kamar farkon magana da su akan barinka fara ƙwallo”.
A hankali ya ɗan furzar da iska yana jin jina kai shima, sai dai a ƙasan ransa yana jin wata nutsuwa mai tarin yawa, dan da gaske ƙwallo abar sonsa ce, burinsa ce tun yana ƙanƙaninsa fiye da kowanne abu da zai iya yi ciki harda zaman office. Takardun da Coach ya fara bashi a farko ya buɗe, ɗan duddubawa yay sai kuma ya ɗago yana kallon Coach ɗin, “Ammah Sir taya kuka samu irin wannan damar haka cikin sauƙi, bayan nasan mutanen kudancin nan namu da iya babbake komai sai su. Su kuma turawan nan da tsantsani akan komai?”.
“Addu’a ne kawai Aliyu, sannan bawai da sauƙin aka samuba ma, an jima ana yaƙin, amma mutuminka dai ne wannan karon ma ya sake shiga ya fita da tsayawar ALLAH data Yousuf muka samu sunan naka ya zama gaba-gaba. Sai su kuma wasanninka da suka ɗan gaggani na baya ya sake ɗaukar hankalinsu matuƙa. Kaga kenan Addu’ar su Ammah tafi gaban komai”.
“Hakane Sir” ya faɗa cikin rauni, sai kuma yay murmushi da kallon Uncle Yousuf da shima ke kallonsa da murmushin. “Uncle kayi haƙuri ka barni na faɗa, wlhy ku na dabbanne a gareni a cikin daban. Har abada harshena bazai gushe wajen muku addu’a ba ku da zuri’arku. Uncle……”
“No no no Aliyu it’s ok! Ya Isa haka ba sai ka cigaba da cewa komai ba, addu’ar nan daka ambata a garemu ita kaɗai ta wadatar, muma bayin kammu bane, ALLAH kaɗai yasan alkairin da ke cikin al’amarin shiyyasa nasarori da yawa suka samu cikin sauƙi. Abinda kawai na sani shine Aliyu kai yaron kirki ne nagartacce da bai kamata ai sakacin da samuwar wata dama irin haka gareku ba, dan arewacin Nigeria na matuƙar buƙatar irinku koma nace Nigeria ko African gaba ɗaya, in sha ALLAHU nan da lokaci ƙalilan sunan Smart Mawashi da ya fara bayyana ƙaddara ta binne sa zai yi zaburar da zata girgiza duniyar ƙwallon ƙafa. Wannan basirar taka bazata wuce a banza ba kamar yanda muke sakaci da ire-iren ku ta hanyar dakushesu a dalilin rashin kulawarmu. Wannan plan ne na shekara kusan biyu da rabi, koda wasa bana son ka kallesa a matsayin dan kana auren ɗiyata ne”.
Murmushi mai faɗi Smart yayi har wasu ƴan ƙwalla na sake tarar masa a ido kaɗan, sai yaji yama kasa cewa komai kawai. Dai-dai nan Lulu ta iso wajen, maganar Uncle Yousuf ta fargar da shi hakan………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣3️⃣
…….Juyawa yay ya kalleta, sai akai sa’a itama ta kallesan suka haɗa ido. Harararsa tai ta ɗauke kanta. Shima sai ya maida nasa gefe kaɗan yana ɗan murmushi. Bata saka hijjab ba amma ta ɗaura Abaya a saman kayan jikinta tare da yane kanta da ɗankwalinta. Tray ɗin hannunta ta ajiye musu fuskarta da murmushi da shagwaɓa bayan ta gaida su ta dubi Uncle Yousuf da faɗin, “Papa i miss you ALLAH”. Dariya Uncle Yousuf yayi da jin daɗin ganinta yanda yake fata tunkan aje ko’ina. Sai da ya karɓi kofin ruwa data zuba masa sannan ya furta, “Mu kewarki ma bamu san yanda zamu misalta ta ba ai Mawaddatan’warahmah. Na gaban goshinki na can yau da ƙyar ya yarda zaije makaranta”.
Murmushi tayi da faɗin “Uncle Please a kawo min shi to mana”.
Shima sai yay ɗan murmushin da faɗin, “Tom ki ƙara hutawa, in dai waɗan nan ne sai kin gaji da su a gidan nan. Dan yanzu haka ma su Auntynki na zuwa”.
Sosai taji farin cikin hakan, duk sai zumuɗi ma ya hanata zama ta juya ciki wai bari yaje ta shirya kafin su iso. Shi da Uncle Yousuf da kallo duk suka bita, yayinda Coach hankalinsa ke kan takardun nan. “Ina fata dai babu wata damuwa ko?”. Uncle Yousuf ya faɗa cikin katse tunanin Smart. Kansa ya jinjina masa cikin sauke numfashi ya ce, “Da sauƙi dai kam. Dan na fahimci wani lokacin tana da sauƙin kai musamman akan lagon mahaifiyarta da ka bani, dan in har zan jingina mata sunanta akan abu zatayi sa babu musu”.
“To Alhamdullah, naji daɗi sosai dan hakan ma ci gaba ne. Ka ƙara haƙuri na haɗaka da aiki, amma nasan nan gaba kaɗan zaka gode min kaima. Dan Mawaddat nada wasu ɓoyayyun al’amura musamman halayen masu ƙyau, a yanda ta tashi taga kanta ne kawai babbar matsalar, sai dai duk da haka tsiwa da jin kanta sama sosai a jininta yake, dan mahaifiyarta tamkar tayi kaki ne ta ajiye, itama haka take kamar wata jinin sarauta wajen izza. Bambanci su kawai ita ta samu tarbiyya fiye data Lulu ne, da kuma kasancewar ita da girmanta ta haura wata ƙasa karatu ba kamar Mawaddat ba. Sai dai fa Aliyu yanzu yaƙin bana Mawaddat bane kawai, sannan ba ita kaɗai bace a filin dagar. Na farko sai munyi haƙuri da Yaya, na biyu Alhaji Sulaiman da ɗansa, dan nasan duk da baya ƙasar nan hankalinsa na nan, kuma gab yake da dawowa tunda jikin Tajuddeen ɗin da sauƙi.”
“Karka damu Uncle Yousuf ku dai ku cigaba da mana addu’a. Daddy kuma insha ALLAH babu komai a tsakanina da shi sai girmamawa, na kuma fahimci son da yake mata ne mai tsanani da tausayinta ke rinjayarsa”.
“To Alhamdullah nagode daka fahimci haka. Yanzu sai ka fara shirin nan da kwanaki zakaje Legos ɗin kamar yanda suka buƙata”.
“ALLAH ya kaimu”.
Da Amin suka amsa su biyun. Da ga haka suka ɗan sake tattaunawa shi da Coach akan abinda ya shafesu na harkar ball ɗin dan yanzu kam zai koma filin daga saboda training, sunja lokaci sosai dan har aka kira sallar azhar kafin su bar gidan su uku suna tsokanarsa da dariya wai yanzu ya koma ɗan 23years. Uncle Yousuf harda faɗin yanzu Lulu ma ta girmesa tunda gashi ma harya fara tsoronta dan yanzu ma dai sai da aka taɓa drama. Dariya yayta yi shi dai abinsa, dan koda ya koma ciki domin kiran Lulun suyi sallama da su Uncle Yousuf a ƙofa ya tsaya saboda gudun karta sake rutsashi. Dan ya manta bai zare key ɗin ba. Kamar kuwa ya sani tayi target ɗinsa akan hakan ALLAH dai ya taimake sa, amma duk da haka sai da tace bafa zai fita ba, sai da Coach ya bata haƙuri akan su Aunty Saliha na zuwa shiyyasa zai fita dan bai kamata su samesa a gidan ba haka akeyi sannan ta haƙura ta barsu, amma yasha harara kamar idanunta zasu faɗo….
Suna barin gidan su Aunty Saliha na isowa, hakan yay matuƙar ɗauke kewar Lulu da sanyata a farin ciki. Sai a yau taga lefenta na wajen Smart. Tayi mamakin ganin kayan da aka kai ɗin da shan jinin jikinta akan anya kuwa babu wani abu a ƙasa da su Uncle Yousuf ɗin ke shirya mata, wai tayaya aure wata ɗaya duk akaima wannan irin kisan kuɗin. Dauriyar dannewa tai dai batace komai ba har suka kammala abinda zasuyi bayan la’asar suka wuce. Suna wucewa kamar wani shiri sai ga Nadiya da wasu ƙawayensu da sukan haɗu a wajen shaye-shayen su, sai dai ita Lulu bawani tana kulasu bane sosai dan itafa dama can ba ma’abociyar shiga sabgar tarkace bace kasancewar ta wayayyar yarinya, ga kuma ƙawaye da ta daɗe da ajiye babinsu a rayuwarta. Ƙoƙarin rufe ƙofar tai tamkar ma bata gansu ba amma Nadiya ta iso da sassarfa ta riƙe cikin roƙo da magiya. Lulu da gaba ɗaya ganin Nadiyar ya sakata jin fusata ta ɗaga hannu ta ɗauketa da mari haggu da dama, sannan ta nunata. “Wannan shine hukuncin da fuskarki zata cigaba da fuskanta a duk lokacin da kikai yunƙurin nuna min ita, Nadiya duk abinda na ajiye tofa idan baki sani ba da ga yau ki sani na ajiyesa ne har abada dan bana jeka ka dawo, FURAR DANƘO NA KE A SHEKARA ANA DAMU BANI FARAU-FARAU. duk ramin da maciji ya sareni sau ɗaya bana ɗaura ƙafata a wajen karo na biyu. Ni nan da kike gani na fiki fiye da abinda kike tunanin kin iya, bana cin amana ba kuma na zama da maci amana, ki fita a rayuwata, dama ke kika sakko kanki cikinta ban ganyyaceki ba”. Da ga haka ta maida ƙofar ta rufe da ƙarfi har sai da duk suka zabura.
“He he he babbar bala’i mai citta da kayan sanyi, wai dama haka yarinyar nan take bata da mutunci? Akan kawai saurayi ya bita inda bata gayyacesa ba take wannan tada jijiyar wuyan, ƴar iska bayan ance mana rainon turai ce wane kalar iskanci ne basayi a can amma zatazo nan tana nuna mana ita wata kamila ce. To wlhy zamu bata mamaki, dan wannan marin da tai miki sai ta fansheshi da abinda har abada kuka bazai bar kwaranya a idanunta ba, zata san ta haɗu da ƴan tasha na asali, dan ƙarshen iskanci a Nigeria aka haifesa da yanke masa cibi aka kuma rainesa a ciki yay girma yay furfura, idan ma ya mutu anan za’a biznesa sai ranar bayyanar judal su tashi tare su haɗa ayari”.
Murmushi takaici Nadiya tai da janye hanunta da har yanzu ke a kan kuncinta tana maida ƙwallar data cika mata ido. Ta ce, “Shuwa Lulu ta wuce duk yanda kike tunaninta, ki kuma iya bakin ki dan ta fiki in dai jidali ne. Lolipop ma tayi bataci riba ba. Ni nai mata laifi dan tun farko ta gargaɗeni akansa amma banji ba, nai mata ma farko tace karna sake na biyu amma na sake kuma, na san nice da laifi dan Lulu ta ƙyautata min a rayuwa, na kuma san bata ƙaunar huɗɗa da maza amma na sake maimaitawa. Shiyyasa nace muku bazan zo ba sai nan gaba ta sake hucewa amma kuka matsa, ga shi abinda sakamakon hakan ya bada kun jamin tozarci…” kafin wani cikinsu ya ce wani abu ta nufi motarta da sukazo ciki ta shiga, bin bayanta sukai da sauri suma duk suka shiga. A guje tabar anguwar damma ba yawan hayaniyar mutane a aria ɗin kasancewar sa babbar anguwa……
__________★
Bayan magrib Smart ya koma gida, ya iske Lulu cike fam da taicin su Nadiya har lokacin. Kasancewar bai san abinda ya faru ba sai ya ɗauka fushi take na daɗewarsa. Dan haka yayta satar kallonta da ga inda yake tsaye dan tunda ya shigo batako ɗaga kai ta kallesa ba balle ya samu sannu da zuwa. Aikinta take tayi a laptop da shan chocolate da su Hussain suka kawo mata lokaci-lokaci. Ice-cream ɗin da ya sayo mata da shawarma ya ajiye gabanta, batare da yayi magana ba shima ya wuce bedroom. Wanka yay har zai kabbara salla sai kuma ta faɗo masa a rai, amma sai ya ture zancenta gefe ya kabbarra sallarsa, sai da ya idar sannan ya miƙe, fitowa yay inda ya sake samunta har yanzu ido a laptop babu alamar ma ko kallon kayan da ya kawo matan tayi. Babu alamar wasa a harshemsa ya ce, “Kinyi sallar magrib da isha’i?”.
Shiru babu alamar zata tanka masa, ya ɗan rumtse idanunsa da sake buɗewa cikin sake kausasa harshe da buɗe deep voice nashi fiye da farko ya sake maimita mata. Yanzu kam dole ta ɗago ta ɗan kallesa, cikin harara ta ce, “Miye naka a ciki idan nayi ko banyi ba? Wai nikam dan ALLAH miyasa kake son shiga min rayuwa da yawa ne haka? Ko gadin rayuwata aka baka ne bani da labari. Bana son damuwa kabar ganin ina ɗaga maka ƙafa ka dinga ganin zaka cigaba da latsani a duk sanda kake so fa, dole ne duk abinda nayi ko baka nan sai na faɗa maka”.
Idanunsa kawai ya zuba mata, sai dai baiyi magana ba sai hannunsa kawai da ya rumtse waje guda alamar ɓacin rai matuƙa tattare da shi amma yana controlling temper ɗinsa. Dan baya son ko sau ɗaya ya ƙwace wajen bayyana mata ɗayan side ɗinsa a yanzu. Tsaye kawai ta gansa a gabanta, batare da yay magana ba ya ɗauke lap-top ɗin gefe gaba ɗayamta ya ɗauka kamar ɗazun. Yanzu kam ba duka ba har da su cizo takai masa amma ko gezau, bai direta ko ina ba sai bathroom ɗin ɗakinsa, dama a farce take, sai hakan ya ƙara tunzurata, sai dai kafin furucin bakinta ya ida fita ya taka mata birki da faɗin, “Shiiiiii!! Idan ki ka sake cewa tak wlhy sai kin sha mamaki yau.” da ga haka ya juya yay ficewarsa ya barta a toilet ɗin. Tsabar rasa abinyi sai kawai ta saki kuka, hawaye sosai tayi kafin tayi alwalar, koda ta fito batako kalla inda yake ba tai ficewarta, shima sai bai ce da ita komai ba dan ya riga ya kai waya ɗakin nata ya ajiye ta yanda in ma batai ba zai gani. Sai dai kuma Alhamdullah, koda ta shiga can ɗin sallar tayi dan da gaske dama batayi magrib ɗin ba, Azhar da la’asar dai da yake aunty Saliha na gidan tare ma sukayi. Bayan ta idar ta jima zaune a wajen tana tunani akan nasihar da Aunty Saliha ta sake mata musamman akan ibada. Da ga baya ta sake fitowa falon, anan ta sameshi kwance. Inda lap-top ɗinta ta ke ta koma ta zauna ta cigaba da harkar gabanta batare data kulashi ba, shima kuma baice mata komai ba yay shiru ne ma a kwancen kamar mai barci yana tunanin abinda ya faru a yinin yau ɗin gaba ɗaya. Sai da ta shagala a abinda take yi yaje ya ɗakko wayarsa, koda ya duba ya ga tayi sallar sai ya sake samun nutsuwa……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣4️⃣
………Haka abubuwa suka cigaba da tafiya a gidan Smart da ɓangaren kwallonsa. Dan matuƙa ya dage da training da kuma kiyaye cin abubuwa tare da miƙama UBANGIJI al’amuransa, harda azumin kwana uku yayi da sadaka. Maganar shaƙuwa ko hirar arziƙi kam tsakaninsa da Lulu babu. Babu mai shiga sabgar wani ta ɓangaren lalama, garama shi wani lokacin yakan ɗan tsokaleta ita kuma tai masifa. Idan lokacin salla yayi kuma ko baya gidan zai tura mata text message akan tayi dan ALLAH, tai ma mahaifiyarta kuma addu’a. Sosai yake karya lagonta da hakan shiyyasa a yanzu kam Alhamdullah da wahala kaga lokacin sallar ma ya shige bata tashi tayi ba, daya turo saƙon ko batai niyya ba zata tashi taje tayi. Idan kuma yana gidan zai mata magana nan ma tayi. Girki ma dai kullum da rigima ake yinsa na safe dana rana idan har yana gidan, idan kuma ya fita na safen kawai akeyi ita dama ba damuwa tai da abincin ba, da dare kuma shi dama ba damuwa yay da cin abinci ba balle yanzu da yake sake ƙoƙarin daidaita jikinsa. Kayan shaye-shaye dai duk da ya toshe ko’ina da samunsu hakan baisa zuciyarsa ta samu nutsuwa ba, a duk motsinta kaffa-kaffa yake yi, ita kuma duk da ta daure kwana biyu a cikar kwana na biyar sai da yanayinta ya canja saboda matuƙa take buƙatar su, ta rage kulashi suyi faɗa, ta zama shiru-shiru, wani lokacin ma yakan shigo gidan ko ɗakinta ya ganta zaune a lungu ta takure kanta cikin damuwa koma tana kuka, sosai take bashi tausayi, dan haka a duk sanda ya ganta a yanayin sai ya zauna yayta mata nasiha ne cikin tausasawa, yana kuma ƙoƙarin bata ruwan addu’oin da malam ya basa a ɓoye batare da ta sani ba, magani ma na nan zuwa da malam ɗin yace zai haɗa mata inasha ALLAH akan shaye-shayen dai. A ɓangaren karatu da suka fara duk da dai suna ɗan kai ruwa rana wasu lokutan kafin ayi, Alhamdullah ya fahimci tana ganewa, dan a ɗan tsukun kwanakin a ɓangaren salla abubuwa da yawa Lulu ta gyara, tana kuma ƙoƙarin riƙe addu’oi. Nacin fita aiki kuma bata daina ba, shi kuma bai kulata ba. Washe garin da suka cika kwana biyar ranar asabar Aunty Bilkisu da Hawwah da Maryam da Asma’u sukazo gidan, ranar yana gida bai fita ba, dan dama fitar tasa dai ba ko yaushe bace ba, ba kuma ta wuce zuwa gidansu, stadium training, sai ɗan kaikawo akan case ɗintan nan na yarinyar nan da yake mata bincike tunda su Uncle Yousuf sun shigar da ƙara court da mahaifiyar yarinyar da kuma taimakon ƴan sanda. Duk sanda ya fita kuma baya yarda ya daɗe idan yayi tunanin ya barta ita kaɗai dan a ɗan zaman sun nan ya fahimci bata son kaɗaici, sai kuma sauran kai kawon da suke da su Coach akan batunsa na abubuwan da suka saura dole da kansa zaiyi. Tarba suka samu ta muntunawa ga Lulu irin wadda su kansu basuyi zato ba, sai suka ji ƙaunar matar ɗan uwan nasu ta ƙara mamayesu. Fargabar da suke ta wataran zai iya aure matarsa ta rabasu da shi ta fita fit a zuciyarsu. Yana ɗaki yana barci hayaniyarsu ta tada shi, bai san kosu waye ba dan haka ya tashi badan barcin ya ishesa ba ya fito, turus yay yana kallonsu, sai bin Lulu daketa faman murmushin yake da kallo, a zuciyarsa kuma yana wani tunani, musamman akan maganar malam da yace tana da ɓoyayyun halaye masu ƙyau, to amma miyasa masu aikin gidansu su take musu duk yanda taso? Kodan su suna a ƙarƙashin ta ne take gani, na biyu ya fahimci bata son kaɗaici sam, dan koshi idan zai fita gidan sai ya ga yanayinta ya canja zuwa damuwa koda bazatace komai ba. Maryam ce ta fara hangosa, cike da jin daɗi ta ce, “Yaya Hydar sannu da fitowa”. Da kai ya amsa mata, yayinda sauran ma duk suka juyo harda Lulu, sai dai kallo ɗaya ta masa ita ta ɗauke nata idon. Falon ya ƙaraso ya zauna, cikin girmamawa ya gaida Aunty Bilkisu, su Hawwah ma suka gaida shi. Daga haka aka ɗan cigaba da hira sai dai basu yarda sunyi wani abinda Lulu zataji a ranta kamar ita barece a cikinsu ba. Wannan abu yayi matuƙar tasiri a zuciyarta, sannan yanda suke girmama juna da shaƙuwarsu da soyayya mai ƙarfi ya matuƙar sata jin kewa da jin inama itama haka take da nata ƴan uwan. Ta kasance cikin farin ciki a wannan yinin, dan ko abinci Maryam da Hawwah ne sukayi basu barta tai komai ba sai Asma’u data gyara gidan, dan wannan shine kema Lulu wahala kuma duk da bata ƙaunar ƙazanta. Ta masa maganar mai aiki yaƙi ce mata komai, shi kuma ba mai aikin ce baiso ba duk da yasan kuɗin biyanta ma a garesa wani abu ne daban, tsoron kar mai aikin ta zame mata ƴar aikar sayo ƙwaya yake shiyyasa yay mata shiru. A lokacin da su Hawwah ke kitchen suna girki Aunty Bilkisu kece masa. “Hydar baka ganin ya kamata kayi haƙuri Hawwah ta koma ɗakinta, mijinta na sonta sannan yana ƙoƙarin sa a kanta, mahaifiyarsa kuma shima tafi ƙarfinsa ne. Tunda su Abba sun bar komai a hannunka ya kamata ayi haƙuri ta koma haka nan ai anja masa kunne, ALLAH tausayi yake ban kullum yana cikin zaryar zuwa gidan nan, ga Nasreen dake damunta kullum ita Abbanta Abbanta, ita kanta Hawwah dauriya kawai takeyi da kuma bazata iya ƙetare maganarka ba, kayi haƙuri ka duba ta koma gidan mijinta kodan halin Umma da bata gajiya da abin faɗa kullum ta ALLAH a gidan nan kan Hawwah, haƙurin shi yafi komai ko ya kikace Mawaddat?”. Ta ƙare maganar tana duban Lulu da ke saurarensu. Jin jina kai Lulu tai da faɗin, “Hakane Aunty, to amma miya kawo matsalar har haka? Sa’id ɗin bashine na gani a wajen bikin nan ba anata kai da kawo da shi?”.
“Shine fa…..” nan ta kwashe komai ta sanarma mata. Sosai Lulu tai mamaki, sai dai kuma hakan baizo mata baƙoba dan sun sha cin karo da irin waɗan nan case ɗin wasu ma sai iyayen mijin sun illata yaran saboda ƙiyayya, wasu ko yaranne fitsararru, sannan kakarsu Dada ita kanta fitinanniyar mace ce da tasan tana ƙuntatama matan kawun nanta matuƙa. Duban Smart tai da faɗin, “To amma shi miyasa bazai zauna yay magana ta fahimta da mahaifiyarsa ba, ko kuma yabar gidan nake ganin hakan zai basu masalaha idan basa ganin juna ai Aunty, ko za’a dinga samun matsalolin ba kamar suna zaune waje ɗaya ba”.
“Kowama haka yake faɗa Mawaddat, to amma maman ce taƙi yarda wai zasu barta a kaɗaici. Shi dai mijinki shi ya kamata yay haƙuri a duba kodan Sa’id ɗin” ta ƙare maganar da kallon Smart.
Shiru kamar bazaice komai ba sai kuma ya ɗan nisa. Cikin ɗage kafaɗa ya ce, “Aunty Bilkisu bawai zaman nata nima namin daɗi bane, sai dai kuma bazan barta ta koma ba haka salin alin, inada shiri nima dan dolene sai mahaifiyar Sa’id ta fahimci kuskurenta ko kuma ya raba musu gidan, inada hikimata na tsaiwa akan hakan dan har mahaifinsa ya dawo sannan”.
Cikin gamsuwa Lulu ta ce, “Hakan da yayi ɗin shine dai-dai, inba hakaba komawar tata haka nan babu wani mataki zai cigaba da bada damar faruwar fiye da haka a tsakaninsu……”
Haka suka cigaba da tattaunawa har su Hawwah suka kammala girki. Wani abu daya saka Lulu farin ciki lokacin da su Aunty Bilkisu sukai zaman cin abincin da suka zuba a tray ɗaya sai ta tsaya kallonsu musamman da Smart ya ɗakko nasa spoon yazo tsakkiyarsu ya zauna yana faɗin “Ni sai a ware ni”. Abune da bata taɓa gani a gidansu ba, itama saita tura baki gaba tace, “Ni baku so naci da ku saboda ba Ammah ta haifoni ba”.
Da sauri aunty Bilkisu ta kamo hanunta ta zaunar kusa da ita kusa da Smart kuma ɗan shine a gefenta, har suna haɗa baki ita da su Hawwah wajen faɗin, “Karkisa Ammah ta dafamu a tukunyarta da jin wannan kalamai”. Murmushi tayi kamar yanda shima Smart ke kallonta ta ƙasan ido yana yi, sai tana mai jinta kamar sabuwar halitta a yau. Lulu da bata damu da abinci ba yau kam saita saki jiki ta ɗan ci. Da son neman magana Smart ya ɗauki naman gabanta, hararsa tayi da tura baki itama ta ɗauki na gabansa batare da tace komai ba, kallonta yay yana ɗan zaro ido ya ce, “Miye kuma na ɗauka min nama Madam?”.
“Nawa daka fara ɗauka naka ne”.
Itama ta faɗa cikin ɗam murguɗa baki kaɗan. Kai kawai ya jinjina alamar zan rama, su dai su Hawwah sai gimtse dariya suke. Can Lulu ta sake ɗaukar naman gaban nasa ta rufe da abinci, sarai ya ganta sai baiyi magana ba sai da ya shammaceta ta ɗakko zata kai baki caraf ya ɗauke sa daga spoon ɗin nata ya lunƙuma baki. “What!” ta faɗa tana kallonsa, miƙewa yay da mata gwalo yabar wajen dan ya ƙoshi daman. Da gudu su Maryam suka tashi suna dariya. Lulu ta dubi Aunty Bilkisu kamar zatayi kuka ta ce, “Aunty kin ganshi ko? Shi baiso a zauna lafiya kullum sai anyi faɗa yake jin daɗi”.
Aunty Bilkisu dake danne dariya da ƙyar ta harari Smart da dafa Lulu da itama ke hararsa ta ce, “Kinga ƙanwata barsa zamu rama. Tsarabar dana kawo takine ke kaɗai nama fasa bashi”. Murmushi tai da sake hararar Smart itama ta masa gwalo da faɗin, “7-6”. Ƙwaɓe fuska ya ɗan yi shima da yin ƙwafa ya ce, “Ki jira game over. Aunty kuma gaskiya ba haka akeyi ba”.
“To ni haka zanyi”. Cewar Aunty Bilkisu tana hararsa. Sai kuma ta kalla Lulu, “Kin san wani abu shi fa dama Hydar akwai zura tun yana yaro, idan aka zuba abinci aka bashi sai yace shi bashi yake so ba na Ammah yake so, idan aka bashi sai kuma yace (Ni wannan ina co) ya sake nuna namu, nan ma a bashi sai ya sake nuna wani nanma yace shi wannan yana co, hankalinsa bazai sake kwanciya ba sai yaga kaf abincin an tara masa gabansa zai bar kunnen kowa ya huta kuma fa ba ci zaiba.
“Kai aunty miye na faɗa mata kuma” Smart ya faɗa cikin shagwaɓa. Aiko mi Lulu zatai inba dariya ba. Sai ta kallesa tace “Ni wannan ina co” ta ƙyalƙyale da dariya. Sai da takai ya kwashi filos ya fara jefa mata ta tashi da gudu tana cigaba da faɗa. Dole aunty Bilkisu ta dara itama tana sake jin ƙaunar Lulun a ranta. Waɗan nan abubuwan sun matuƙar ɗauke ma Lulu kewa da sakata a farin ciki a wannan yinin, yayinda gefe ɗaya ta takurama Smart da faɗin ‘Ni wannan ina co’ har bayan tafiyarsu. Shima sai abun ya koma bashi dariya dan ya fahimci ta samu abin yi………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣5️⃣
……..Washe gari bayan ya dawo motsa jikin safe da yake fita yace ta shirya zasu fita, da mamaki ta dubi agogo da faɗin, “Da sassafen nan? Ko 8 fa batai ba”.
Shima agogon ya kalla sai kuma ya dubeta. “Ina ganin kafin mu kammala shiryawan tara ma zata iyayi, dan inada abune mai muhimmanci shiyyasa nake son mu fita da wuri”.
“Wai ina to zamuje?”.
“Idan mun fita ai zaki gani, ke dai ki shirya”. Ya faɗa yana ficewa, kitchen ya nufa ya sake ɗaukar ruwa ya sha sannan ya nufi bedroom ɗinsa ya cire kayan motsa jikin dake jikinsa ya faɗa wanka. Itama a ɓangaren Lulun wankan ta tashi ta shiga, dan dama dai tana duba karatun da ya ƙara mata ne kafin fitarsa training. Harga ALLAH tana jin daɗi da farin cikin karatun da sukeyi na addini, abinda kuma ke sake zaburar da ita akan hakan watarana akan wani case an gayyaceta hira a gidan wani tv tare da wani lawyer da basa shiri sam saboda duk karon da tai da shi a shari’a sai ta kaisa ƙasa. A cikin hirar kawai ɗan jaridar sai ya sakko wata magana data shafi addini, amma sai ta kasa amsa masa dan bata sani ba, sai shi lawyer ɗin ya amsa da karsashi da son nuna isa har yana mata shaguɓe akan bata da ilimin addini. Abin ya mata ciwo, tun a lokacin kuma tayi ƙudirin fara neman ilimin sai dai bata san tayaya zatai hakan ba, sannan bata da shaƙuwa da wani a ƴan uwanta da zata iya kawo zancen ta yanda za’a fahimceta, na biyu rashin barin abu a rai da take da shi ya sata tattara abin ta ajiye gefe ta cigaba da sabgoginta. To bayan fara karatun nan da Smart ke koya matan sai ta fara fahimtar abubuwa da dama, sannan tana jin wani nutsuwa da jinta daban da dacan duk da bawani nisa sukai ba can sosai, dan ma dai ƙwaƙwalwarta mai saurin ɗaukar abu ta taimaka mata matuƙa. Kamar yanda ya faɗa sun kai kusan ƙarfe taran, dan sanda ya fito bayan ya shirya koda yaga kayan data saka kai tsaye yace mata ta sakesu. Taso masa gardama amma sai yace tayi haƙuri gidansu fa zai kaita ta gaida su Ammah kuma can zata yini sai dare. A take yaga farin cikinta ya bayyana, dan ita dai tunda Asma’u suka bata labarin yanda Ammah ke sonta da bibiyar abinda take yi sai take jin ɗokantuwa da sake ganin Ammah ɗin duk da a waccan zaman na kwana ɗaya da aka kaita gidansu bazata ƙarar da fuskar kowa ba. Kanta tsaye ta ce, “To dan ALLAH zoka tayani zaɓen wanda zasuyi”.
Idanu kawai ya zuba mata sai kuma ya saki murmushi zuciyarsa na ayyana masa abubuwa da dama. Baiyi zaton zata nuna ɗokin sake zuwa gidansu ba tunda ta kwana a ciki taga yanda yake. Ya fahimci gane wacece ita kai tsaye abunne mai wahalar gaske, dan idan ya gama haddace nan ya buɗe mata sabon shafi sai yaga nan ɗin ma dai akwai abubuwan ban mamaki a cikinsa fiye dana baya daya baro.
Da kansa ya zaɓa mata kayan kamar yanda ta buƙata. Atamfa mai ƙyau da akaima ɗinkin zani da riga, sai hijjab. Anan ne ta ɓata fuska da ɗauke hijjab ɗin gefe ta ajiye ta ɗauka gyale. Zaiyi magana ta marairaice fuska. Shiru yay baice mata komai ba ganin gyalen nada girma. Sai kuma wajen ɗaura zani ma wata sabuwa. Dan Lulu bata iya ba, da tayi-tayi taga ta kasa saita shiga ƙwala masa kira dan sanda zata saka kayan catai sai dai ya fita, shi kuma baiyi musu ba ya fita ya tsaya a ƙofa. Kiran nasa da tai ya sakashi dawowa. Cikin ɓata fuska ta ce, “A canja wasu gaskiya”.
“Saboda mi”.
“Toni na iya ɗaura zani ne”.
Dariya taso ƙwace masa amma ya danne. Ya ƙarasa shigowa ciki yana faɗin, “Kin yarda na ɗaura miki?”.
Shiru tai kamar mai tunani, sai kuma ta ɗan hararesa da faɗin, “To wlhy ka rufe idonka, dan inka kallan ban yafe ba”.
“Oh hakama zaki ce daga taimako?”.
Baki taɗan murguɗa batace komai ba. Shi kuma sai yay murmushi kawai da ƙarasowa inda taken dan bai son ya biye mata Coach nacan na jiransa. Da taimakonsa ta ɗaura zanin duk da anata masa masifar ya rufe ido kuma karya taɓa mata jiki, duk da yana da abubuwan faɗa baice komai ba shi dai. Ɗaurin ɗan kwali ma bata iya ba. Cikin dafe kai ya ce, “Naga takaina, na auri bahaushiya a zahiri amma bata da banbanci da turawa ni Aliyun Ammah”.
Harara ta zuba masa ta figi handbag ɗin ta da mayafi ta fice. Sai wata leda da bai san ko minene a ciki ba hartayi gaba ta dawo ta ɗauki kayarta. Bayanta yabi yana dariya da faɗin, “8-6 kenan”.
Sai da ta hararesa ta ce, “Kama isa. Wlhy 7-6 na sani”.
“K matsalata da ke rinto, garama ki yarda kinyi game over”.
“Never give up wlhy, mai sama da hundred ne yay wining”.
Ta amsa masa nan ma tana hararsa. Ita ta fara fita, shi kuma ya kashe kayan wutar dan an haɗa musu tv yanzu ya kullo ƙofar ya fito. A jikin motarta ya ganta tsaye, sai ya ɗauke kansa ya nufi gate. “Ina kuma zaka je?”. Ta faɗa tana kafesa da idanun ta. Kansa tsaye ya bata amsa batare da ya juyo ba. “Zan sama mana Napep mana”.
Da mamaki ta ce, “Napep kuma? Ita kuma wannan motar fa? Ni malam bana son ƙauyanci kazo mu wuce danni kam bana hawa Napep. Bamma taɓaba”.
“Sai ki fara da ga yau”.
Ya amsa mata yana yin gaba. Tana nan tsaye mamaki da jinjina girman kansa na cimata zuciya, dan ita abinda ta fassara kawai kenan a al’amarin nasa sai gashi ya dawo, baice da ita komai ba ya ɗauka handbag ɗinta da ledar nan ya dubeta da faɗin, “Muje”.
“Aliyu!”.
Ta faɗa cikin kaiwa ƙarshen mamakinsa. Amma sai ya ɗaga mata hannu da nuna ƙofa alamar suje. “Sai dai ka tafi kai ɗaya dan gaskiya bazan shiga Napep ba, kaje zan sameka acan”.
Wani ɗan lumshe idanunsa yay na gundura da maganar a taƙaice ya ce, “Zan ɗauke ki har ƙofar gidan ba ruwana. Dan na faɗa miki ana jirana ko”.
Yanda yay magana a dake babu alamar wasa ya sake sata tsira masa ido. Sai kuma shawarar da zuciyarta ta bata na ta bishin koba komai yau ta ɗan fita tasha iska ya sata ture komai gefe tai gaba yabi bayanta yana sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya. Lulu naji na gani a karo na farko na tarihin rayuwarta ta shiga Napep. Sai kuma taji hakan ya sakata a farin ciki batare da tayi zato ba, ga wata iska mai daɗi na rsatsaka tako ina. Sannan kai-kawon mutane da yanda kowa ke sha’aninsa musamman masu tallar abubuwa akan titi yay matuƙar ɗaukar hankalinta da sakata jin tausayinsu. A karon farko zuciyarta ta bata talaka na wahala akan taro da kwabo a ƙasar nan. Wani ɗan yaro da ke tallar papcorn ta yafito da hannu sanda suke tsayawa cikin wani gajeren holdup. Bazai wuce shekara goma sha huɗu ba.
“Hajiya guggurun na nawa kike so?”.
Yaron ya faɗa yana ƙoƙarin yago ledan guggurun a jikin ƴan uwansa. Dakatar da shi tai da faɗin, “No ba shi nake so ba. Miya hanaka zuwa makaranta kake nan kan titi?”.
Ɗan jim yaron yay kamar bazaiyi magana ba, sai kuma ya kalleta ya sake kallon Smart da ke kallonsu kawai batare da ya tanka ba. Muryarsa da alamar damuwa ya ce, “An koroni ne dan Abbana bai biya ba tunda na gama aji uku wai baida kuɗi.”
Idanu ta zaro na mamaki. Sai kuma ta ce, “Kaga yanzu a titi muke ina ne gidanku?”.
“A kwana uku muke”.
Handbag ɗinta ta ɗauka ta ciro jota da pen ta miƙa masa. “Kaga samun Number wayan mamanka anan idan ka sani”.
“Sai dai na yayata, Umman mu wayanta ya faɗa ruwa”.
“Idan ba damuwa sakamun ta yayar taka”. Da murna sauri-sauri yaron ya saka dan an sakesu. Ya miƙa mata. Amsa tai da miƙa masa 2k tana murmushi. Da ga haka suka wuce. Mai Napep da ke kallon komai yay ƴar dariya da faɗin, “Hajjaju idan irin waɗan nan yaran kikace zakiyita amsar lambarsu dan basuje makaranta ba aiko zaki amshi sama da miliyan goma a garin nan. Bayan ƴan gari akwai ƴan cirani kamarsa-kamarsa ba adadi. Su dama sauƙi tunda suna neman na kansu ai, wasu kamarsun rashin karatun kesa abokan banza jan ra’ayinsu su faɗa ƙwacen waya da tare yaran da aka aika a lungu su amshe kuɗin. Ko kiga sun faɗa harkar shaye-shaye yara ƙanana kaga yaro na zuƙar maka tabar wiwi ƴan iskan banza iyayensu sun haifa mana bala’i”.
Wani irin harbawa zuciyar Lulu tai akan zancensa na ƙarshe. Sai taji bakinta yayi nauyi tama gagara cewa komai, sai ɗagowa da tai ta ɗan dubi Smart da yay kicin-kicin da fuska yanzu kam yana ma mai napep ɗin wani shegen kallo. Aiko sai taji mai Napep yay tsitt yana ɗan satar kallon Smart ɗin ta mirror. Har suka iso fagge zantukan na mata juya-juya a zuciya da kartar mata rai. Ba komai ya kawo hakan ba gareta sai tuna itama fa ta fara shaye-shaye ne tana da shekara goma sha uku a duniya. Har ƙofar gida aka kaisu, anguwar da mutane sosai kasancewar Lahadi ne wasu basa fita, ganin yanda akai musu caa da idanu yana biyan mai Napep ɗin yaja hanunta suka shige ciki. Sun samu yaran duk suna nan, basu kai ga wucewa islamiyya ba gidan caka-kai caka-kai. Sai shigowarsa ta sa mafi yawan yaran yin shiru, masu aiki suka maida hankalinsu ga aikin da sukeyi. Asma’u ce dake shanyar kayan Ammah da suke wankewa ita da Maryam ta taho da gudu tana faɗin, “Aunty Oyoyo Oyoyo. Sassanyan murmushi Lulu ta saki ta riƙo hannun Asma’u da ta noƙe gab da zata iso saboda hararar da Smart yay mata ta fasa rungume Lulu da tai niyya, hararsa tai da jawo Asma’un jikjnta dan sarai taga hararar da yayma yarinyar. Maryam ma tasowa tai da fara’arta tana musu sannu da zuwa tare da amsar kayan hanun Yayan nata. Sai suma sauran yaran dake a tsakar gidan duk suka shima musu sannu da zuwa da gaishesu. Suna ganin sun shige falon Ammah kowa ya nufi kaima uwarsa rahoto dan duk suna cikin ɗakunansu aunty Amarya ce kawai a wajen Abba dan yau itace da shi. Sun sami Ammah na sallar walha, sai Nasreen da ke kuka mamanta ta daketa, yayinda ita kuma Hawwahn ke ƙoƙarin saka turaren wuta a rushin da ta ɗibo………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣6️⃣
……..Itama cikin farin ciki take musu sannu da zuwa, yayinda Lulu ke amsawa tana nufar Nasreen. “Oh oh mi akaima wannan princess ɗin ne haka take ɓarnar hawayenta masu tsada?”. Ta faɗa tana ɗaga Nasreen, zama tai ta ɗaurata saman cinyarta. Itako ta lafe cike da shagwaɓa da kuka ta ce, “Ba Mommy bace ta daken dan na kira Abbana a wayanta”.
“Ayya Mommy ita bata san mun ɗan ara bane muji muryan Abba. Barta daina kukan bazamu bata chocolate ɗinmu ba”. Tai maganar da share hawayen Nasreen ta ɗauka handbag ɗinta ta ciro chocolate biyu masu daɗi da tsada ta baima Nasreen. Tuni ta fashe da murnar dariya ta kaima kuncinta sumbata cike da farin ciki, sai kuma ta ɗaga musu chocolate ɗin tanai musu gwalo. Hakan ya bama Lulu dariya ta saki murmushi, suma duk sai suka fashe da dariya ƙasa-ƙasa. Dai-dai nan Ammah ta idar da sallanta, batai doguwar Addu’a ba ta juyo fuskarta da murmushi mai ƙyatarwa. Akan Smart da ke zaune kujerar kusa da inda take sallan ta sauke, sai kuma ta maida ga Lulu. Kafin tace wani abu ya saukko a kujerar ya zauna kusa da ita yana gaisheta, ganin haka yasa itama Lulu sakkowa da ga kujerar ta zauna ƙasan carpet ɗin da ke a share tas ga ƙamshi mai daɗi na tashi a falon ta ce, “Ammah ina kwana”. Da sauri Ammah ta girgiza mata kai da miƙa mata hannu murmushin ɗunbin farin cikinta na sake bayyana ta ce, “A’a zonan ɗiyata kinji, taso maza taso gareni”.
Abin mamaki sai Lulu ta samu kanta dajin kunyar Ammah. Da ƙyar ta iya miƙewa ta nufo inda take, zata zauna ɗan nesa kaɗan nan ma Ammah ta riƙo mata hannu ta zaunar da ita jikinta sosai. Ajiyar zuciya Lulu ta saki hawaye na ciko mata ido, amma sai ta daure kanta a ƙasa ta sake gaida Ammah a karo na biyu. Shi Smart ma da abin ya girmesa kasare kawai yay yana kallonsu. Ammah ta riƙo hanunta cikin nata tana amsawa da kulawa.tare da ɗorawa da faɗin, “Ki saki jikinki ɗiyar albarka nan gidanku ne, ni ɗin ban son ki ɗaukeni mamar mijinki mamaki ce dan yanzu kinfi Hydar matsayi a wajena….”
Cikin waro idanu da ƴar shagwaɓa ya ce, “Ammah! Hakama zaki ce ina babanki ɗin?”.
“Kai tafi can ai photo copy ne ba original ba wake ta taka. Anata sabon ɗa waketa tsohon ɗa”.
Dariya su Hawwah suka saka, Lulu ta ɗago ta masa gwalo da nuna masa 8-6 da hannu. Lips ɗinsa ya cije da ƙaramar harara. A dai-dai nan Mama ta shigo tanama baƙuwa lale marhabun. Itama sai Lulu ta gaidata da girmamawa, Mama ta amsa da fara’a tana sanya mata albarka, dan ita dai barta da rashin mutuncinta idan ya motsa ko Umma ta tunzurata. Amma tanada kirki a lokuta da dama, sannan bata saka ƴaƴa a kishinsu inba taƙure ba.
Yaranne suka shiga shigowa ɗaya bayan ɗaya suna gaidata kamar yanda Mama ta basu umarni, sai dai a ƴaƴan Umma Mubarak ne kawai ya shigo cike da zumuɗi, dan yaso zuwa gaida amaryar yayan tasu Umma ta taka musu birki akan duk wanda yaje koda a bayan idonta saita tsine masa. Wannan girmamawa da Lulu taga an mata ya matuƙar birgeta, (tana son a girmamata a nuna mata ita mutumce mai daraja) koda Umma ta leƙo itama a gatsine wai tana mata sannu da zuwa da ɗan habaicin basu fara shiga ɗakunan su ba Lulu ba fahimtar komai tayi ba. Hasalima kallo ɗaya taima Umman ta duƙar da kanta dan haka kawai take jin Ammah ta mamaye mata ko’ina. Bata taba jin nauyin mutum da kwarjini kamar yanda takeji akan Ammah ba. Ga tsantsar soyayyar ta data hanga a cikin idanun dattijuwar yasata jin wani irin ƙaunarta ta musamman. Smart da shima yake matuƙar jin farin cikin nutsuwar da yaga Lulu tayi a gaban Ammah ya ce, “Da nasan haka za’amun a gidan nan daban zo ba. Amma ba koma a bani shayi nasha nai gaba. Zaku nemeni ne”.
“Wake buƙatarka balle ya nemeka anan”. Cewar Ammah da murmushi. Fuska ya shagwaɓe da faɗin, “Ammah! Ammah gara dai ki tarairayeni dan da tsohuwar zuma ake magani”.
“Ga wanda bai sani ba ba”.
Ammah ta bashi amsa.
“Shike nan na daina magana. Hawwah bani shayi na ƙara gaba, itama fa ku nema mata abinci bamu karyaba muka fito dan zumuɗinta”.
Ammah ta ce, “Kai Hydar dan ganganci. Shine kuma maimakon ka kira waya tunkan ku taho a ɗaura muku”.
“Haba Ammah sai kace wasu baƙi”.
“Baƙine mana. Tunda wannan ne karo na farko data fara marabtarmu dan wancan ba’a sakashi a lissafi. Ɗiyata mi kike son ci”.
Ƙasa Lulu ta ƙara yi da kanta tana girgizawa da faɗin, “Ammah bana jin yunwa ma, abarshi har sai anjima”.
“A’a bazai yiwu ba Mawaddatan’warahmah. Ƙarfe goma harta gota ace sai kuma anjima”.
“Ammah bason cin abinci take ba shiyyasa. Idan kika biye nata ma daga nan har dare zata iya kaiwa”. Smart dake ƙoƙarin kai shayin da Hawwah ta kawo masa bakinsa ya faɗa. Ɗan harararsa Lulu tai ƙasa-ƙasa bata dai ce komai ba. Shi kuma yay mata murmushin da take kira na mugunta.
Yana kammalawa ya miƙe da faɗin shi zaije ya gaida Abba ya wuce, sai anjima zai dawo. Addu’a Ammah tai masa da ta ratsa zuciyar Lulu matuƙa harta tsira musu ido. Karo na biyu yaji wani abu ya tsikarar mata zuciya game da ilimin addini, sai kewar mahaifiya data ratsata, itama fa da Mah-mahn ta nada rai da haka zata dinga mata ko? Sai hawaye suka cika mata idanu. Su Ammah daba lura sukai ba Smart ta ɗan dubeta cikin jin nauyin Ammah ya ce, “Madam na barku lafiya, duk abinda kike buƙata karkiyi fillanci Ammah taki ce.”
Kanta ta jin jina masa tana ƙoƙarin maida hawayenta. Da ga haka ya fice ya barsu….
Cikin ƙanƙanin lokaci aka shiryama Lulu breakfast, yayinda gidan ya ɗauki shiru su Asma’u ma sun wuce makaranta. Ammah nata janta da taɗi itako tana bata amsa cike da kunya har Hawwah ta kammala tazo ta zauna. Sai Ammah tace suje ɗaki ko zata fi sakewa ta karya kafin suje ta gaida Abba da matan gidan dan yau dai ba fita zaiyi ba. Jin haka yasa Lulu cewa bari taje ta gaida Abban dan bata jin yunwa. Hakan yasa Ammah jin daɗi, dan haka ta miƙe da kanta domin rakata wajen Abban. Hawwah kuma ta shiga tattare kayan tana maidawa ɗakinsu…
Sosai Abbah yayma sabuwar surukar tasa tarbar mutuntawa kamar yanda yake ma sauran. Yayinda Lulu shima ta kasa ko kallonsa dan tsohon ya mata kwarjini sosai. Shima ta gaidashi da girmamawa ya amsa mata da kulawa da sanya albarka. Sannan ya ɗora da addu’a zama lafiya a gare su Ammah na amsawa da Amin cikin murmushi. Basu jima sosai ba dan sunga Lulun dai kunyarsu ta sata kamar takura suka fito bayan ta ajiye masa leda madaidaiciya mai ɗauke da turarruka masu tsada da ƙamshi, sai agogo. Da sauri Abbah yace, “A’a ɗiyata maza zoki ɗauka. Gaidamun ma da kuka zo kawai ya wadatar mun kumayi farin ciki”. Marairaice fuska Lulu da kanta ke a ƙasa tai da faɗin, “Abbah dan ALLAH karkace haka. Mu albarkanku muke nema, indai bazan sayama Daddy abu dan neman albarka ya dawo min da shi ba kaima haka nake fata daga gareka”. Abba dake murmushi sai ya jinjina kansa da nisawa. Ya ce, “ALLAH yay miki albarka. ALLAH ya tsare gabanki da bayanki….” ya dinga jera mata addu’oi masu ratsa zuciya Ammah na tayashi kafin suka fito.
Anan kam saita kira Hawwah akan tazo ta raka Lulu kowane ɗaki. Hawwah ce tai mata rakkiya, inda suka iske Umma cike fam, amma saboda shawarar da Hajiya Naqiba data kira ta labartama mata zuwan su Lulun yasata dannewa ta tarbeta da fara’ar yaƙe, ita kuma Lulun sai ta kasa sakin jiki da ita dan ita kam dai haka kawai taji Ummah batai mata ba, basu wani jimaba Lulu ta ajiye mata ƙaramar leda ta miƙe, sai hakan kuma ya sake zafar Umma. Ɗakin Mama ma an mata tarba ta mutuntawa, nan ma sai sukafi ɗakin Umma daɗewa, dan duk da Mama taji hassadar kasancewar wannan zukeƙiyar yarinya ƴar masu kuɗi ba wani acikin ƴaƴanta ya samu ba ta danne a ranta ko a fuska bata nuna ba, sai godiyar ledar da Lulun ta ajiye mata ya shiga jerawa. Ɗakin aunty amarya kam tarba suka samu kamar wata ƙawa. Dan tsokanarta ma taitayi suna dariya. Sunfi jimawa anan fiye da ko’ina kafin su koma ɗakin Ammah bayan itama ta ajiye mata ledar, bakuma komai bane aciki sai kayan turaren wuta data ɗiba musu da su cin-cin. Itama Ammah ta kawo mata harda turmin zani biyu su Asma’u kuwa kayan kwalliya ta basu jiya da sukaje. Basu zauna a falo ba suka nufi bedroom ɗin su Hawwah ɗin inda ta maida break fast. Duk da Hawwah zata iya ɗan girmar Lulu da ko shekara biyu ne jikinta ta saki da matar yayan nasu, hakan sai ya saka Lulu sakewa abunta dan wayayyace dama kai babu duhu. Duk da ba son cin abincin take ba sai gashi ta saki jiki sunci tare da Hawwah suna hira cikin mutuntawa, anan ne ma Lulu ta samu damar sake jin matsalar Hawwah ɗin sosai, a ranta kuma ta ɗauki ƙudirin taimaka mata, dan haka ta amshi address ɗin gidan nata a cikin hikima batare da Hawwahn ta fahimta ba. Bayan sunyi sallar azhar falo suka dawo wajen Ammah, cikin hikima taita jan Lulu a jiki ganin bata sakewa idan suna tare, da yake abune daga cikin abinda take ƙishirwar samu sai gashi ta saki jikin nata fiye da yanda sukai zato, dan hirar tasu ne ta karkata akan yanda matsalolin fyaɗe ke ƙara yawaita da yanda wasu ma yaran kan rasa ransu a take ko a cutar da su ta hanyar saka musu cuta, da yanda wasu iyayen kan rasa ransu adalilin hakan kosan ɓoyewa saboda kar duniya taji ƴaƴan su tozarta da su kansu. Lulu ta ce, “Wlhy Ammah nakanji kamar na dinga kashe irin waɗan nan aladun da hannuna, akwai case ɗin wata yarinya da har yanzu yake cimun rai duk da shegen na prison kusan shekara uku kenan, danni duk wanda nasan na samu nasarar alƙali ya turashi prison akan wannan laifin cigaba nake da bibiyasu a prison ɗin dan karma ayi amfani da wata dama a sakesu ina nan baki buɗe. Yarinyar tana nan ta zama mahaukaciya kamar yanda Nanny ɗina ta kasance kafin mutuwarta….”
Wasu irin hawaye suka zubo mata masu azabar zafi saboda tuna mata da abinda ya shuɗe kuma yake sosa mata zuciya da zama sanadin komai da ake kallon zagaye da rayuwarta a yanzu………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣7️⃣
……..Yanda take kuma ya tadama Ammah hankali matuƙa, ta dawo kusa da ita da jawota jikinta ta rungume tana jin itama hawayen na cika mata idanu. Yanda Lulu ke kukan nan zai tabbatar maka al’amarin na matuƙar taɓa mata zuciya, dan har Hawwah sai da tai hawaye. Sosai Ammah taji ƙarin ƙaunar Lulu a zuciyarta. Sai da tai shiru sannan ta fara mata nasiha da bata addu’oi akan ta dage ta dingayi da yawaita karatun Alkur’ani hakan zai dinga rage mata nauyin zuciya, dan masu irin ayyukansu saboda yanda suke tara abubuwan ɓacin rai da damuwar al’umma daga ƙarshe sai kiga sun kamu da hawan jini dana ciwon zuciya. Sosai yanda Ammah ke jero addu’oi a bakinta taji ta sake birgeta da kwaɗayin akan samun ilimin addini. A haka su Asma’u suka shigo ƙarfe biyu. Da mamaki Ammah ke dubansu dan tasan dai sai biyar suke dawowa daga islamiyya duk ranar weekend. Hawwah ta ce, “Kukuma fa naga kun dawo?”. Kallon juna sukayi kafin Maryam tace, “Adda haddace bamu iya ba shine muka gudo, kin san dai malam Jabeer ba sauƙi wlhy”.
Ammah data tsira musu ido tace, “Duk karatun da kukai ɗazun da asuba. Kudai faɗi wani ba wannan ɗin ba. Wai Maryam yaushe ma kika fara ƙarya?”.
Ƙasa Maryam tai da kanta tana shafa ƙeya, Asma’u dake ƙara rakuɓewa jikin kujera ta ce, “Ammah gaskiya da gaskiya dai saboda Aunty muka gudo, kinga fa yini zatayi amma mu banda mu. ALLAH muna son muma mu yini tare da ita shine mukai shiri tare da Adda Maryam idan akai salla muyima Malam Jabeer ƙaryar zamu rakaki asibiti”.
Hawwah dake dariya tace, “ALLAH ya shiryeku Ammahn kukai ma sharrin ciwo kenan?”.
“A’a wlhy mu bamuce kowa ba, kawai dai munce zamu rakata asibiti”.
“Kuma ya yarda? Bayan nasan Malam Jabeer da shegen bin ƙwanƙwanto”.
Dariya Asma’u tai tana kallon Maryam, ita kuma ta harareta alamar dai akwai wata a ƙasa. “Munafukai mi kuke ɓoyewa?”. Cewar Hawwah tana kallonsu cikin waro ido. Alamar zip Asma’u taima bakinta da faɗin “Ba ruwana ba’a bakina ba”. Lulu da ke murmushi ta ce, “Haba Auta bamu musha mana”.
“Aunty ba faɗar bane matsalar, sai kun gudu gidajenku ta jibgan a ɗaki ko Ammah bazata bari ta sani ba”. Ranƙwashi kuwa Maryam takai mata. Da gudu tabar wajen tana dariya. “Sonta yake ya kasa gaya mata, gashi kuma ya tsaya kallon ruwa kwaɗo yay masa ƙafa. Dan ga wani tauraro mai babban haske ya faso kai da ƙarfinsa”. Binta Maryan tayi suka shige ɗaki da gudu. Kai kawai Ammah ta girgiza da faɗin, “ALLAH ya shiryeku”. Yayinda Hawwah da ke dariya ta ce, “A gama ɓoye-ɓoyen intai wari maji ai”. Lulu dai murmushi takeyi dan komansu burgeta yake yi. Bakomai ya jawo hakan ba kuwa sai yanayin rayuwar data tashi a ciki ita da nata ƴan uwan. Bayan su Maryam sun cire Uniform suma falon suka dawo aka ɗora hira, anan sukaci abincin da aunty Amarya ta gama, bayan sallar la’asar Maryam tai zaman yima Lulu kitso. Dan nakan Hawwah ta gani ya burgeta ta tambaya duk da ba son kitso take ba. Jin Maryam ce tayi sai tace itama aimata ko kaɗan. Shine sukai zamanyi suna cigaba da hira harda Ammah. Nasreen da suka dawo daga makaranta tana zaune a cinyar Lulu suna shan chocolate dan itama shazumamun ce kamar Lulun. Sallamar Smart ta sakasu tsagaita dariyar da sukeyi dan Asma’u ce ke kwaikwayon Muryar malaminsu Jabeer dake son Maryam wai idan ya ganta har ƙara maƙewa yake yi. Akan Lulu ya fara sauke idanunsa kafin yabi sauran da kallo, ya ƙarasa takowa cikin falon yana kaiwa zaune da faɗin, “Miyay muku daɗi haka kuke kwasar dariya har tsakar gida kun cikama mutane kunne? Ammah duk sun zagayeki sun dameki”.
Cikin murmushi ta ce, “A’a basu damen ba Hydar, ai ko kurama da ƴaƴanta take wasa a jeji. Sai yanzu muke ganin ka”.
“Wllhy ki bari dai Ammah. Da ga wani waje mai nisa muke fa, kin san Ahmad da shegen kutse-kutse can wani ƙauye ya samo gona zai gyara yay gidan gona a wajen shine fa mukaje dubawa”.
“Kai masha ALLAH, ai haka mukeso mu kuyita shiga irin hakan dan nan gaba kaɗan kune manyan goben.”
Murmushi yay cikin jinjina kansa. Kafin ya maida hankali ga ƙannensa da ke gaishesa. Idon Ammah ya sa Lulu faɗin, “Sannu da dawowa”. Sai da ya maimaita kalmomin guda uku a zuciyarsa yana mai ɗan kafeta da kallo, sai kuma ya janye shima cikin basarwa ya ce, “Yauwa ya gidan”.
Abinci Asma’u taje ta kawo masa, sai cewa yay ta maida baya jin yunwa, garama in sunada fura dan yasan dai Ammah bata rabo da ita. Asma’u tace masa akwai, taje ta ɗibo masa a fridge ta kawo masa. Daga haka suka cigaba da hirarsu Lokaci-lokaci yana satar kallon Lulu da akema kitso masu ƙyau. Wajen shida ya kalla agogo da faɗin, “Ku wannan kitson yaushe zaku gama shi har mu wuce? Gashi ina son mu biya ta wani wajen”.
“Ina? Ai ni nan zan kwana yi tafiyarka”. Cewar Lulu da iya gaskiyarta. Murmushi Ammah tayi, yayinda Smart dake mata kallon mamaki ya ce, “Kwana fa? Kin manta gobe Monday zakiyi resuming office?”.
“Ba damuwa jibi naje”.
Murna su Asma’u suka fara yi zata kwana. Ya hararesu duk sai suka nutsu. Ammah dai bata ce komai ba har sai bayan sallar magrib da ya shigo ya sameta a ɗaki, lokacin su suna can ɗakin suna tasu sallar. Zama yay kusa da Ammah, hakan yasata yin addu’a ta rufe Alkur’anin. “Ba dai tafiyarba ko?”.
“Da haka nake so dai ta shirya, da anyi isha’i sai mu wuce dan ina son mu biya ta gaida Kakanta ɗazun Uncle Yousuf ke faɗamin baya jin daɗi ya dawo daga Legos ɗazun, gashi kuma tana batun kwana anan”.
“Karka damu zan mata magana. Amma Aliyu sai nake ganin akwai wani ɓoyayyen al’amari a rayuwar yarinyar nan dake damunta, na fahimci hakanne a ɗan firarmu da ita ta ɗazun. Sannan bata son kaɗaici, dan ta roƙeni na baku Asma’u ta koma can da zama. Danace mata Abbanku bazai yarda ba ina kula da ita sai da idonta ya cika da hawaye. Mizai hana a ɗan samo mata ko tsohuwa haka da zasu zauna tare, sannan kai kuma ka ƙara ƙaimi wajen janta a jiki dan ka fahimci minene damuwarta. Ko yaya ta sanar maka itama zataji nauyin ya ragu mata a zuciya. Ashe mahaifiyarta bata raye kuma?”.
“Ta rasu, tana haihuwarta. Inasha ALLAH zan yi iya ƙoƙarina”.
“ALLAHU akbar. ALLAH ya gafarta mata. Wlhy duk sai yarinyar ta sake bani tausayi. Gata da sauƙin kai da sanin darajar mutane. Sai kuma yanda na fahimta akan aikin nan nata kamar zafinta akan al’amarin fyaɗe nada alaƙa da wani abu daya sosa ranta gaskiya. Ya kamata dai ka zama mai haƙuri da dinga ƙarfafata”.
“Insha ALLAHU Ammah zan yi iya ƙoƙarina. Batun Asma’u kuma haƙuri zakuyi ta koma can ɗin tunda tana son hakan. Kodan ma tafiyar nan dake tunkarowa.”
“To bazance A’a ba, amma ka samu Abbanku da maganar kadai sanshi. In akan tafiyane kuwa bazai yiwu dama a barta ita ɗaya ba. Ko ita da Asma’u kawai dole cikin samarin nan wani ya koma can ya dinga kwana da su”.
“Hakan ma yayi Ammah. Duk yanda kikace haka za’yin”.
Sun ɗan ƙara tattaunawa akan abinda ya shafesu musamman akan Hawwah, kiran sallar isha’i ya sashi tashi ya fita. Bayan ya dawo sai da Ammah ta lallaɓa Lulu da wayo sannan ta yarda su tafi. Yanda take zubama Ammah ɗin shagwaɓa sai Smart ya zama ɗan kallo. Dan mamakin yanda tai bala’in sakin jiki da Ammahn yake yi har irin haka a ƙanƙanin lokaci. Koda tajema su Umma sallama har yanzu akwai alamar takaicin ƙyautukan data raba musu ɗazun a tattare da ita. Dan kusan ma a tashin hankali ta yini, ga surukar jiya-jiya a gida daga zuwa tana neman fara haskawa, yarinya da baƙin wayo. Ai zama bai ganta ba, dan kuwa kamar ta kashe maciji ne bata dare kansa ba kasancewar Lulu matsayin surukar gidan nan na nufin disashe tauraron ƴaƴanta da ake gani sama dana kowa. Oho Lulu ba damuwa da sabgar da ba’a sakata ba gareta, dan haka ita bata wani fahimci mi Umman ke ciki ba, dan ko kallon su Huwaila dake falon batai ba. Haka kawai jininta dana Umma baizo ɗaya ba, da ƙyar ma ta yarda ta biyo Smart ɗin suka shigo da tace yaje ita zata je ɗakin Aunty Amarya ya sameta ya nuna mata dole ta shiga ko’ina suyi musu sallama. Ganin babu wasa a tattare da shi yasata bin nasa badan taso ba. Daga wajen Umma sai ɗakin Mama. Nan ma basu jimaba suka fito, nan ko Mama ta bata alawar madara da Hannatu keyi ta saidawa. Hakama aunty amarya ta bata farar data soya mata da rana har kwano biyu. Aiko taji daɗi tanata godiya. Abba ma sunyo masa sallama ya haɗa Lulu da tsarabar zuma da mazarƙwaila kasancewar sa masoyinsu yana ajiyewa. Sai da zasu shiga napep Maryam ta ajiye mata ledar tsarabar Ammah. Duk sai Lulu taji ƙaunar bayin ALLAHN nan na sake ratsata. Shi kansa Smart yaji daɗin wannan karamci da sukai mata. Kasancewar mai Napep ɗin ɗan anguwarsu ne zai kaisu har gida da inda ma zasuje kai tsaye ya nufi Nasarawa G.R.A dan Smart ya riga ya sanar masa tun kan Lulu ta fito. Ganin inda suka nufo ya sata jin farin ciki, a Napep ɗin suka bar kayan suka shiga cikin gidan na Alhaji Sufi Ado Garko. Sun sami yaran gidan da jikoki da yawa, inda kowa yay musu ca aga yaya Lulun ta koma. Sai kuma suka ganta fes har wani ƴar ƙiba kamar ta ƙara musu ma su a ido. Alhaji Garko dake kallonsu da murmushi ya nunama Aliyu kusa da shi. Maimakon hakan sai ya zauna a ƙasa kusa da ƙafafunsa ya gaidashi cikin girmamawa da tambayar yaya jiki. Da kulawa ya amsa masa da sanya albarka. Dada kam sama-sama ta amsa masa tana masa hararar ƙasan ido Lulu na jikinta lafe. Ya gaisa da sauran wanda suke ɗakin suma, daga haka yaja bakinsa yay shiru sai Baba ya takalesa da magana ko tsokana ne yake ɗan murmushi koya bada amsa a taƙaice. Kusan awansu biyu sukai shirin wucewa, anan ne Dada ke cema Lulun “Ku bari sai anjima mana tunda dai mota ce kuma daga nan guda kukai”. Batare da Lulu ta kawo komai a ranta ba ta ce, “Dada a Napep muke fa, babu daɗi mun barsa a waje kusan awa biyu. Kuyi haƙuri zan dawo gobe in sha ALLAHU”.
A zafafe Dada ta ce, “Napep kuma? To ina motocin naki? Kodan shi baida motar hawan dan bakin ciki irin na talaka kema bazaki hau ba? Kamarki jikar Garko family a garin nan da hawa Napep…”
Yanda Dadan ke maganar a zafafe da ɗaga murya kowa naji ya saka Lulu duban inda Smart yake, sai kuma ta dubi Dada zatayi magana cikin ɓata fuska amma ta dakatar da ita……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣8️⃣
…….Itama dakatar da itan abinda tai niyyar sake faɗan da tai tana duban Smart da yay kamar baima san akansa ake maganar ba Baba yayi rai ɓace. “Wai miye haka kuma ban son ƙaranta fa. Ke Mawaddat tashi ku wuce gida.”
Miƙewa Lulu tayi kamar yanda Smart ya miƙe babu alamar komai da zaka iya fahimta a fuskarsa. Sai ma kallon Baban yay cikin girmamawa yay masa sallama tare da sauran jama’ar ɗakin. Wasu sun amsa masa wasu ko nata faman taɓe baki ƙasa-ƙasa yanda Baba bazai gani ba. Koda yayma Dada sallama bata kulashi ba, shima kuma bai nuna ya damu ba yay ficewarsa. Suna fita cikin ƙarfin halin rashin jin daɗin jiki Baba ya balbale Dada da faɗa, ta inda yake shiga batanan yake fita ba har sai da ta koma bashi hakuri duk da dai fa ta ciki na ciki…..
Lulu tata satar kallon Smart da tunanin zaice wani abu akan abinda Dadar ta masa amma har sukazo gida baida alamar cewa komai. Bayan ya sallami mai napep ya buɗe musu suka shiga, gaba ɗaya kayan na’a hannunsa har handbag ɗinta ma. Har ɗaki yakai mata kayan sannan ya fita zuwa nashi ya barta da binsa da kallo. Harga ALLAH bataji daɗin abinda Dada tai masa ba. Dan koba komai ita ai daga gidansu take. An kuma girmamata an mutuntata kamar a goyata. Kuma fa duk ta bama Dadan labari a taƙaice amma ta aikata masa hakan. ALLAH ya kaimu gobe zataje sai tai mata magana dan bata son haka. Duk da bata son shi bata kuma tunanin zama da shi bayan na wata ɗayan nan bazata so a wulaƙantashi ba dan itama dai da taje gidansu ba’a wulaƙantatan ba ai. Da wannan tunanin ta shiga wanka.
Shima a can wankan ya shiga, sai dai duk da ya danne abinda Dadan ta masa yay masa ciwo sosai. Sai dai ya zaɓi shanyewa dan koba komai taci darajar Baba. Sannan bazai taɓa wulaƙantata ba kasancewarta kaka ga Lulu. Bayan yay wankan ya fito shafa’i da wutri yayi sannan ya fito. Shayi ya haɗa a kofi biyu ya nufi ɗakin Lulu da su. Kwance ya sameta rigingine ta ƙurama fanka ido da alamun damuwa tattare da ita. Dan ko sallamar sa bataji ba sam. Zama yay a bakin gadon da yin gyaran murya sannan ta dawo firgigit, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya da tashi zaune. Idanunsa ya janye daga kallon ta yana haɗiyar busashen yawun daya tokare maƙoshinsa dan shi yasan abinda idonsa ya gani kasancewar rigar jikinta ta barci ce mai santsi. Itama sai ta jawo ƴar saman rigar data ajiye gefe ta ɗora akan wadda ke jikinta dan ƙarama ce ma da kaɗan ta wuce mata cinya. Taji kunyar ganin nata a hakan amma dai ta basar. Shayin ya miƙa mata shima cikin basarwar, amsa tai idanunta a kansa, ganin babu dai damuwar da take tunanin gani ya sata jan ajiyar zuciya da faɗin, “Thanks.” kansa kawai ya ɗan jinjina mata. Numfashi ta sauke a hankali sai kuma ta sake dubansa da faɗin, “Kayi haƙuri da abinda Dada tayi, ni ban faɗa mata da wani manufa ba. Ita haka take tana da faɗa ne sosai”.
Murmushi yay a karo na farko, sai kuma ya ɗan kafeta da idanunsa da suka canja launi kaɗan. cikin tsokana ya ce, “Wajenta kika koyi faɗa kenan?“. Hararsa tayi da ɗan murguɗa baki. Ya sake sakin murmushi da kai shayinsa baki. “Karki damu ai nima kakatace. Ni ban ɗauki abinda tai ɗin komai ba. Yanzu ma magana nazo muyi”. Bai bata damar sake cewa komai ba akan Dadan ya shiga bata bayanan daya ɗan tattara mata game da case ɗin yarinyar can dake a asibiti, sai kawai ji yay ta rungumesa a bazata. Wani irin mahaukacin bugawa zuciyar Smart tayi, jinin jikinsa ya shiga yamutsawa tsigar jikinsa duk ta mimmiƙe. Lulu da bata kawo komai da wata manufa ba game da abinda tai ɗin ba ta ɗago tare da lakace masa hanci tana kallonsa da murmushi ta kashe masa ido ɗaya. Sai ya samu kansa da sakin murmushi yana mai lumshe idanunsa.
Komawa tai ta zauna da faɗin, “Ashe kana da kirki wani lokacin”. Shi dariya ma ta bashi, sai dai baice komai ba kan hakan ya sake yin murmushi kawai da ɗakko maganar fitarta aiki gobe idan ALLAH ya kaimu ko zai samu daidaiton abinda ke tsikarinsa. Nasiha ya fara mata cikin kwantar da kai da muryarsa data koma ƙasan maƙoshi, tare da faɗa mata dokokinsa akan yanda yake buƙatar ta dinga fita”. Da farko taso daurewa, sai dai jin dokar fita da hijjab har ƙasa ya sata dubansa cikin tura baki ta ce.
“Hijjab har ƙasa? Ni ce zan saka hijjab har ƙasa, impossible hakan ta kasance, idan mafarki kake ka farka. Wai miyasa kai baka so a zauna lafiya ga son nuna ma mutane gadara akan rayuwarsu? Ka mance wannan auren ba aure bane balle ka dinga tursasani yin abubuwan nan. To ni ko auren gaskiya ace nakeyi bazan zama a ƙarƙashin takalmin namiji ya takani ba, idan zamuyi rayuwa cikin kowa yanada freedom fine, balle wannan auren. Please ka bari kwanakin nan su cika muna masu mutunta juna. Ni harka ma ɓatamin rai na”.
Kallonta kawai yake yi batare daya fahimci mima take nufi ba, sai dai baice komai ba harta gama. (karku manta Smart bai san da tsarin auren yarjejeniya ba, Uncle Yousuf Daddy da Lulu kawai ya shuka a haka). Tashi tai ta bar masa wajen ta shige toilet dan bata buƙatar abinda zai ɓata mata farin cikin data samu yau a wajen ƴan uwansa, shima sai ya mike ya fita a ransa yana faɗin (akwai ƙura kenan kuwa gobe. Dan shikam wannan tsarinsa ne, ko yau ma ya barta ta fitane da gyalen dan kawai tare zasu fitan, ya kuma san daga gida sai gida kawai….
WASHE GARI ta tashi da ɗokin fita aikinta, musamman zancen shiga kotu da zasu fara yau akan case ɗin nan. Tsaf ta gama shirinta, sai uban ƙamshi take zubawa dan ta baza turaren nata. Tana ƙoƙarin ɗaura igiyar takalmanta ya shigo ɗakin. Sanye yake da jallabiya ash da bata kai masa har ƙasa ba sosai, sannan gajeren hannu ne da ita. A jikin ƙofar ya jingina tare da harɗe hannayensa a ƙirji ya zuba mata idanu kawai. Ƙin ɗagowa tai duk da taji shigowar tasa har sai da ta kammala. Koda ta ɗago ɗin ma kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta tana miƙewa. Da ga sama har ƙasa ya sake ƙare mata kallo. Yayinda ita kuma ta ƙarasa tattare kayanta ta nufo ƙofar kanta tsaye. Kallonsa tai kamar yanda shima yake kallon nata, a dake ta ce, “Ina kwana bani hanya”.
Maimakon amsa mata sai ya ɗan kauda idanun nasa a kanta ka ɗan batare da ya motsa ba ko ya tanka. Ta fahimci so yake su maimaita na waccan ranar, ita kuma ba haka take buƙata ba. Dan haka ta danne abinda ke taso mata da ɗan kwantar da murya ta ce, “Please Hydar 9:30 ne shiga court fa, kuma ka sani”.
Cikin husky voice ya ce, “Idan baƙyason rasa shari’ar ko makarar go and change your dresses. Na faɗa miki duk abinda bakina ya furta shine nake buƙata kuma bana canjawa da ga ra’ayina akan duk abinda na riga na tsara.”
Cikin ɓacin ran da ya fara yunƙuro mata ta ce, “Aliyu!!…”
Hannu ya ɗaga mata babu alamar wasa a tattare da shi. Muryarsa vary deep and vary clear ya ce, “Na yanke kuma na zartar, bi kawai shine masalaha Mawaddat. Ke matata ce, nace bana buƙata to bana buƙatar. Kiyi kawai kodan kuma ki sami yanda kike so mu kuma zauna lafiya”.
Jitai jiri ma na neman kamar ɗibarta. Amma sai batace komai ba tai masa wani irin kallo mai ƙunshe da abubuwa masu yawa ta juya kawai ta ajiye kayan hannunta a saman gadon. Komawa tai wadrobe ta ɗakko hijjab zata saka kawai, amma sai ta tsinkayi muryarsa yana faɗin, “Kayan duk zaki canja zuwa wasu, bana son wannan turaren kuma idan zaki fita, idan zaki saka a gida fine ko zakiyi wanka da shine ba babu damuwa a gareni. Sakawa a fita ne dai bana so dan haramunne ma a gareki ba faɗa ta bace.” bata tanka masa ba, sai kayan data ɗauka ta nufi toilet dan taga baida alamar fita, ita kuma taci alwashin bazata kulashi ba a yanzu saboda abinda ke a gabanta. Tsaf ta sake shiryawa cikin wasu kayan ta saka hijjab ɗin ta fito, sai ya samu kansa da kafeta da ido. Dan tayi ƙyau matuƙa a cikin hijjab ɗin fiye da waccan ranar. Shi da kansa ya ɗibar mata kayan yay gaba tabisa a baya tana taunar lips na danne masifar dake cimata zuciya. Baya ya ajiye mata kayan tare da miƙa mata hannu alamar ta bashi key ɗin motar dake hanunta.
Rai a ɓace ta ce, “Bana buƙata”.
“Kema kin san aikina ne ai hakan”. Ya faɗa babu wasa shima a tattare da shi. “Aina faɗa maka na kore ka”.
“Ban koru ba, dan bake kika ɗauke ni aiki ba ai ko”. Ya sake bata amsa a dake yana zare key ɗin tare da jan hanunta ya tura ta kujerar kusa da driver ya maida ya rufe. Zagayawa yay shima mazaunin drivern. Koda yaje gaban gate sai da ya fita ya buɗe sannan ya zo ya fita da motar ya sake komawa ya rufe gidan sannan. Tunda suka ɗauki hanya babu wanda ya tankama wani, gara shi ma ya miƙa mata ƙaramin flaks da ya haɗa mata tea a ciki. Kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa tana harararsa. Murmushi kawai yay batare da yace komai ba ya maida hankalinsa ga tuƙinsa. Kai tsaye office ya kaita, inda suka samu abokan aikinta suna tsaiwar jiranta duk da safiya ce sosai. Motar na shigowa suka shiga mata marhabun su Zainab na mata spry da ƙyalkyali mai ƙamshi da ga shi har ita. A take aka shiga musu murnar auren. Kamar yanda ya dake yana amsawa itama sai ta dake tana amsawa. Sunci kusan mintina goma a wajen kafin Zainab ta kwashi kayanta suka wuce office, shi kuma sai ya fito bayan sun ɗan yi magana da security ɗin nan da a yanzu suka saba sosai ya samu napep ya shiga ya koma gida………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣9️⃣
…….Alhamdullah yau Lulu zata ce kasancewar abubuwa sun tafi mata yanda take so. Dan duk da zaman shari’ar yau aka fara Alhmdllh tana hango nasara a cikinta. Bayan barin kotu da Hassan yazo ya kaita da kansa office ya sake maidata, ta ɗan taɓa aiki bayan sallar azhar ta fito. Tana jan mota ta fita Security ɗin nan ya dannama Smart waya ya sanar masa. Godiya yay masa sannan shima yay kiran wanda ya saka ya dinga bibiyar masa ita akan yabi bayanta da napep ɗin. Kai tsaye anguwar da mijin Hawwah yake ta nufa, da tambaya ta isa gidansu Sa’id. Mai Napep da ke binta ya kirasa ya sanar masa. Sosai Smart yay mamakin abinda ya kaita, har ya dinga jin son yazo amma dai ya dake da ƙyar dan son ganin iya gudun ruwanta. Sama-sama ta gaishe da maigadin tare da tambayarsa ko hajiyar gidan na nan? Amsa mata yay da eh cikin washe haƙora. Fuska ta yamutse cike da izzarta ta ce, “Sanar mata tana da baƙuwa”. Babu musu ya amsa mata da to yana nufar cikin gidan. Mintinan baifi uku ba sai gashi ya dawo ya ce ance ta shiga.
Kallon gidan ta dingayi side by side tana taɓe baki, a irin dukiya ta gidansu gidan su Sa’id ɗin ba komai bane ba, sai dai ba laifi suma dai da gani akwai kuɗin sai dai ko kama ƙafarsu basu isa yi ba. Ƙofar da take ƙyautata zaton falon gidan kenan ta nufa, cikin sa’a ma sai ta hango wata yarinya tsaye kamar tana kuka da alama mai aiki ce, isowarta kusa da ita ya sata daina kukan ta risina ta gaisheta. Sau ɗaya ta amsa mata ta ɗauke kanta. Yarinyar ce ta mata iso cikin falon, babbane sosai ya kumaji ɗirka-ɗirkan kujeru kamar bana dattijuwa ba. Kallo ɗaya taima matar dake zaune a falon ta fahimci itace mamar mijin Hawwah ɗin, dan ko’a ido ka kalleta kasan za’a zuba da ita kam. Zama tai kanta tsaye tun kan ma ace ta zauna, maman Sa’id dai kallonta take alamar rashin sani, duk da Lulu ta fahimci hakan sai ta basar, cikin ɗaukar kan nan nata na isa da ƙasaita ta ce, “Hajiya barka da rana. Sunana Barrister Mawaddat Isma’il Jiƙamshi.”
Sai da zuciyar maman Sa’id ta motsa jin ƴar waye, sannan sunan kansa na Mawaddat ɗin duk mai bibiyar harkokin mata a fanin fyaɗe dole zai santa, ita kanta dama tunanin ina tasan wannan fuskar takeyi. Lulu data lura da hakan ta cigaba da faɗin, “A yanzu haka matar Aliyu M. Idris Mawashi yayan matar ɗanki dan bana tunanin kin halarci bikin sati ɗaya daya shige”.
Gaba ɗaya Mama duk sai ma taji ta daburce, dan tabbas Sa’id yata roƙarta zuwa bikin amma tace bazataje ba dan ba’a gayyaceta ba, koma an gayyacetan bazataje bikin matsiyata ba dan tasan dai bai wuce tuwo da waina da zoɓo ba. Harga ALLAH bata san ɗiyar wa Aliyun ya aura ba. Da ɗan jimami ta ce, “Da gaske kece matar Aliyun?”.
Lulu dake mata wani kallo a yamutse ta amsa da, “Oh baki yarda bane? Zaki iya tambayar ɗanki ni yanzu ba wannan ne ya kawoni ba. Nazo nan ne game da case ɗinki da Hawwah, kinyi ƙoƙarin zuba mata mai dake saman wuta da nufin ƙonata, ba kuma wannan ne karo na farko ba da hakan ta faru. Kinci arziƙin ɗanki shiyyasa banzo da police ba a yanzu haka domin kamaki. Amma nazo da kalaman gargaɗi a gareki a karo na farko. Su iyayenta sun barki saboda jin nauyin karamcin ɗanki. To ni kuma a matsayina na mai kare hakkin mata kuma matar Yayanta bazan iya barinki ba. Kin haifi Sa’id ba kin haliccesa bane, yana kuma da damar yin aure tunda bake zaki auresa bane, matsayinki daban matsayin uwa matsayin matarsa daban matsayin mata. Nan gidan aurenki ne, shi kuma nan gidan da aka haifesa ne, kina zaune da mijinki lafiya dan haka itama ki barta ta zauna da nata mijin lafiya. Wannan takardar da kike gani na tattara dukan abubuwan da kikai mata ne, tare da bincike mai yawa akanki a wajen ƴan anguwa da ƴan uwanki dana mijinki, kuma sun bani duk wani information a kanki har ma wanda bakiyi zato ba. Haka ma mijinki nayi waya da shi yanzu haka, dan haka kina da zaɓi biyu zaki saka hannu zan saka hannu Sa’id zai saka hannu hakama Hawwah da sharaɗin zaki fita rayuwar aurensu ki zauna a matsayinki na mahaifiyarsa, zakuma subar wannan gidan su koma nasu, sannan kije da kanki gidansu ki bata haƙuri ki bama iyayenta haƙuri. Zaɓi na biyu ƙin amincewa da shawarar farko na shigar da wannan case ɗin kotu mu zuba shari’a wlhy har sai na kaiki jail dan har video ke gareni na randa kika kusa kasheta a dalilin hankaɗota daga saman upstairs gashi”. Ta ɗaga mata wayar tana mai playing video ɗin, jikin maman Sa’id ya fara rawa, Lulu ta sake shiga wani ta ce, “Ga kuma na randa kika watsa mata ruwan shayi harta ƙone a wuya shima”. Sosai Lulu taga ruɗewa a idanun Mama. Tai murmushi da kaɗa kanta cike da isa. “Ba waɗannan kawai ne ba, akwai wasu tari-tari kuma duk Hawwahn ke ajiyesu, bata nuna bane saboda mutuncin ɗanki. Amma ni yanzu na shirya fiddosu a gaban alƙali. Kin san dai mijinki siyasa yake yi har yana shirin fitowa takara a shekara mai zuwa ko, sannan yayanki a yanzu haka ɗan majalissa ne, to a dalilinki duk zan iya tarwatsa wannan damammakin, dan bayan kasancewa jinin Jiƙamshi jinin Alhaji Sufi Ado Garko nake kuma. Sai ki zaɓa na baki nan da kwanaki uku kacal. Na barki lafiya”. Ta faɗa tana miƙewa murmushi ɗauke da fuskarta ta ɗaga mata yatsu biyu tai ficewarta. Sosai jikin maman Sa’id ke rawa da kakkarwa. Dan kuwa Lulu ta daketa ne a inda taji zafi sosai. Videos ɗin nan sun matuƙar tayar mata da hankali, har tana mamakin yaushe Hawwah duk ta ɗaukesu batare da ita ta sani ba. Na biyu matsayin Lulu da hatsabibancinta akan shari’ar duk da ta saka a gaba. Na uku zancen siyasar mijinta da tai matuƙar ƙwallafama rai da buri a yanzu tare da matsayin ɗan uwanta da shima take taƙama da tinƙaho da shi a duk inda ta shiga. Idan wannan damar duk ta kufce musu ai ta shiga uku wlhy, dan za’a mata dariya matuƙa. Itafa dama kishiyar uwar yarinyar nan ce ke sake tunzurata akan tsanarta (Umma), duk da dai dama bata sonta kasancewarta ƴar talakawa, dan taso ace Sa’id yay auren kece raini ne na ƙwarya tabi ƙwarya. Amma ya ƙare da auren ƴar malam shehu……
Lulu data fita da ƙayataccen murmushi a fuska ta shige motar tare da yin reverse tabar angur da gudu dan ita kam akwai wauta da mota. Mai Napep ɗin nan dai na biye da ita. Ganin sun ɗauki hanyar Nasara G.R.A yasa shi kiran Smart ya sanar masa. Koda suka iso gidan na Garko daka ɗan nesa ya tsaya, yayinda ita aka buɗe mata gate ta shige ciki. Yau ma da mutane a gidan, sai dai kusan duk matan kawunan ta ne, suma ɗin dai wanda basa fita aiki ne. Ta samu Baba na barci saboda allura da akai masa, hakan ya bama Dada dake cika na batsewa wa matan ƴaƴan nata jan Lulu suka shige ƙuryar ɗaki. Dan fa ita tun jiya ranta a ɓace yake da batun zuwansu a napep. Balbale lulun tai da masifa, ita kuma ta tsaya tana kallonta da mamaki, sai da takai inda take so har tai shiru sannan Lulu ta taɓe baki. “To wai ni kuwa Dada dan ALLAH miye na damuwa anan, shiga napep ɗin shi minene a cikinsa. Kinbi kin saka ma kanki damuwa”.
“Ya bazan sakama kaina damuwa ba Mawaddat. Kamarki ace kina hawa Napep. To ai ko uwarki datai irin wannan ƙaddararren auren naki bai kai naki watsewa da lalacewa ba. Shi wai cikakken ɗan iska ma, an bashi abinda zai riƙeki har yace baya buƙata. Ke anya kuwa yaron nan ba asiri yay miki ba kuwa?”.
Dariya Lulu ta kwashe da shi a karo na farko, ta ce, “Ho Dada tamu, Aliyun ne zai min asiri. To wlhy bara na faɗa miki ma shi ustazu ne. Dama cakikai girman kai ya hanashi amsa sai na yarda. Amma ba asiri ba. Yo ni koma asirin ne ina ruwana ma, iyakaci lokaci na cika zan ƙara gaba babu abinda asirinsa zaimun ballema ni nasan ba asirin bane. Kuma nidai ki daina zagar min miji dan nima ƴan uwansa basu zagan ba sai ma girmamani da mutuntani da nuna min soyayya sukeyi”.
Dada data saki baki tana kallonta ta ce, “Iyyeee a lallai Mawaddat kinyi baki, harni kike gayama wannan zantukan. To inba asiri ba ubanmi zai kaiki auren yaron dake matsayin driver ɗinki. Ko ƙyan nasa ne ya ruɗeki da waɗan nan shegun idanun nasa kamar na ƴan maye. Dubeki fa wai kece da saka hijjabi yau kamar wata tsohuwa. Yo koni dana haifi uwarki na ninkaki shekaru bazan saka wannan abun har ƙasa na fita ba”.
Baki Lulu ta taɓe tana miƙawa, “Dada bazaki gane ba ke dai. Ya kike so nayi? ya rantse in ban saka ba bazan fito ba gashi inada shari’a mai muhimmanci. Wlhy taurin kan Aliyun nan ya wuce duk yanda kike tsammani. Bar ganinsa yana wani sissine kan nan shegen kansa ne.”
“A to lallai na sake yarda yaron nan asiri yay miki wlhy, ke yanzu duk yanda na sankin nan da rashin ɗaukar raini har kece taurin kan wani ɗa namiji zai girgiza ki ko ya baki tsoro da saki laushi haka a cikin sati ɗaya kacal. Dolene na miƙe tsaye dan wlhy koma miza’ai sai na rabaki da shegen yaron nan dan baza’a sake maimaita abinda ya faru akan uwarki ba. ALLAH dai yasa baki miƙa masa kanki ba ya lalube shegen”.
Dariya Lulu tai harda kwanciya, sai kuma ta ɗago cikin dariyar dai ta ce, “Ke kam Dada inda ace a zamanin baya kikazo irinku ne bakwa musulinta da wuri ga riƙe gaba har ƙarshen numfashi. Indai aurena ne ki kwantar da hankalinki bamai daɗewa bane, sati biyu ya rage ana uku na koma free. Sannan kina damuna da habaici akan Daddy na da Mamana, idan na tambayeki kuma kiƙi faɗa min, kin kuma hana kowa gayamin. Mi Daddyna yay miki ne kike jin haushinsa haka, idan dan yaƙi baki riƙona ne ba gashi yanzu na dawo kina ganina ba”.
“Ke ni ƙyaleni shashasha ba ganewa zakiyi ba. Ni ina tambayarki wani abu ya shiga tsakaninku ne? Sannan kince nanda sati biyu, kin fa sani a duhu”………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣0️⃣
……..Shiru kamar Lulu bazatace komai ba, sai kuma taɗan taɓe baki da ɗage kafaɗa. Cikin rashin damuwa da kallon abinda zatayi ɗin a wani abu ta kwashe komai dangane da auren contract da Uncle Yousuf ya sanar mata saboda kar Baba yay mata auren dole ta sanarma Dada. Ta kuma faɗa mata ita babu abinda Aliyu yama taɓa nuna yana so a gareta, shiyyasa ma take ɗan ganin girmansa”.
Salati Dada keyi a zuciya tana tsinema Uncle Yousuf, wato sunyi hakanne dan kar Lulu ta auri jikanta dake gadon asibiti. To lallai idan sun san wata ai basu san wataba kuwa. A zahiri kam bata nunama Lulu komai ba, tunda dama dai bugar cikinta take. Abinka da tsohuwar mace gashi taji abinda batai zato ba, Lulu kuwa har yanzu yarinya ce fa, dan ma ALLAH ya bata ilimi da kaifin basira, sannan ga yanayin rainon data tashi irin waɗan nan makirce-makircen na tsoffin matan ƙasar hausa ba gane kansu take ba. Sun cigaba da hira da Dada data ajiye maganar Smart har sai da Baba ya farka suka fito, Lulu taje ta dubashi. Ta jima a wajensa kafin ta tafi dan tana son komawa office. Mai Napep ɗin nan da yay zaman jiranta dan Uncle Yousuf ya bashi napep ɗin ne domin kawai bibiyar Lulun. Smart ya kirashi har sau biyu amma yana sanar masa tana a ciki bata fito ba. Da ta fito kuma yay kiransa ya gaya masa. Hakama da suka koma office. Ta sake zaman kusan awa biyu a office kafin ta fito Zainab biye da ita d kayayyakinta. Bayan ta saka mata ta sanar da ita gobe ta fito da wuri dan akwai wasu baƙin da take saran zasu zo nemanta. Da girmamawa Zainab ɗin ta amsa mata, ita kuma ta shiga mota sai gida. Sai dai ta tsaya wajen wani mai bread ta saya. Koda mai napep ya sanarma Smart bai kawo komai a ransa ba game da sayen bread.
(Ni dai nace Humm lulun mu fa ta wuce da saninka Smarty 😂😜).
★★★……
Tun shigowarsu cikin Saloon ɗin nata tai kamar wadda ta suma. Ba ita kaɗai ba hatta matan dake wajen ana musu ayyuka mabanbanta kallon mamaki suke musu dan kowa dai yasan anan mata kawai akema aiki banda maza. MM Atik Kumo ya katsema Nadiya tunani da faɗin, “Hello girl”.
Nannauyan nufashi ta kawo da dubansa, cikin ƙarfin hali da in ina ta ce, “Ranka ya daɗe lafiya dai?”.
“Ita ta kawomu. Ko zamu iya ganinki a waje?”. Asim ya bata amsa kai tsaye. Ƴan shagon ta duba, ganin duk sun zuba musu idanu yasata cewa, “Okay muje”. Su suka fara fita sannan tabi bayansu tana jan ƙaramin tsaki da gargaɗar yaranta su cigaba da ayyukan gabansu. A cikin motar su ta samesu, MM Atik dake zaune mazaunin driver yay mata nuni da ta shiga ciki itama. Batai musu ba ya buɗe ta shiga, bayan ta rufe ta gaishesu. Asim ne kawai ya amsa mata MM Atik kam tambaya ya jeho mata na cewar “Yaya ƙawarki?”
Numfashi ta ɗan furzar da gimtse fuska, a taƙaice ta ce, “Ban san yaya take ba dan bama tare yanzu. Tun a waccan ranar bamu sake kasancewa tare ba”.
“Saboda mi?”.
Cewar MM Atik ɗin yana jiyowa gaba ɗayansa gareta. “Hummm saboda naje da su Alhaji Baita wannan get together ɗin fa. Kasan na faɗa maka Lulu ta tsani maza, shiyyasa nake kallon kamar aljani ya aureta ne shiyyasa. Yanzu haka ma zancen bikinta sai gani nai an ɗaura mata aure wai da driver ɗin nan nata a tv, hakama dinner ɗin ta gani kawai nayi ana nunawa duk da kuwa na bata haƙuri ta waya da duk hanyar data dace amma taƙi saurarena”.
Murmushi MM Atik yayi damin hango irin ruwan bala’in datai masa a randa ya fara ganinta. Nadiyar ya kalla da faɗin, “Ai masifa bata mata wahala. Bar batun auren driver dan kuwa muna ganin da manufa tayisa, sakamakon son gujema auren Hon. Nakowa da wannan ɗan uwan nata Tajuddeen Sulaiman Garko. Ba ita kawai ba nima naji haushin ganinku da tsoffin nan a wancan ranar, kawai dai na miki shiru ne”. Shiru Nadiya batace komai ba akan hakan, shima sai ya cigaba da faɗin, “Manta abinda ya faru ya faru ya wuce, yanzu sabon dil nake son mu ƙulla”.
“Nami kuma kenan?”.
“Akan ƙawar taki dai, dan bazan iya haƙura ba.”
“Abu mai wahala kenan, dan ta yanke alaƙarmu, tare da gargaɗin nisantar ta. Nasan halinta kuma sarai idan ta faɗi abu har cikin ranta ne. Abu ne mai matuƙar wahala Lulu ta sake kallona balle har na shiga jikinta”.
“Zamu iya amfani da wata ai, amma ya zama ke zakina controlling nata”. Cewar Asim.
Kai Nadiya ta jinjina da faɗin, “Wai babbar magana. Na fahimci bakusan wacece Lulu ba. Kubar ganinta haka batajin magana tasan mitakeyi. Sannan koni kaina nasha wahala kafin mu fara abota gaskiya, dan bata da saurin sakewa da mutane, sannan ba kowa ke iya haƙuri da halin Lulu ba”.
“Karki damu inhar aka jajirce wannan ba komai bane ba. Sannan kema fa akan aikin nan zakija manda. Dan a yanzu haka zamu sauke miki miliyan ɗaya kafin ma aikin ya fara”.
Sosai Nadiya ta zaro ido waje, ranta fal farin ciki ta ce, “Yanzu yaya kuke so ayi?”.
Kallon juna sukai da murmushi, kafin Asim ya miƙa mata card da faɗin, “Ki samemu a wannan address ɗin zuwa anjima”.
“Wannan yafi komai sauƙi”.
Ta faɗa tana amsar card ɗin……..
_______________★
Kwanaki uku kenan da fara fitar Lulu aiki, kullum kuma Smart ke kaita office da safe sannan shima ya koma gidan yay shirin tashi fitar a Napep. Idan ko fita ta kamata a yinin mai Napep ɗin nan da bata san da shi ba na biye da ita. Duk kuma inda ta saka ƙafa ana sanar masa. A lissafinsa dai babu wani abu dake faruwa, dan ranar farko ta sayi bread wanda bai san a tsakkiyarsa aka saka mata kayan shaye-shayen ta ba, kamar yanda takeyi sai zata kwanta tasha hakan tayi, shiyyasa bai gane komai ba sai ya ɗauka kawai gajiyar aikin data koma ce tunda tayi ƴar zirga-zirga. Washe gari dai yaga ta tashi a tsayenta bakamar kwana biyu datai wani sukuku ba. Rana ta biyu ma sai da tai amfani da dabarun nasu ta amsa, hakama jiya. Yau cikon kwana na uku yaso ya ɗan fara tsarguwa, amma dai baice komai ba. Yana son mata tambaya akan zuwa gidan su Sa’id sai kuma dai yay shiru. Sai kuma gashi a yau yana tare da Coach kira ya sameshi da ga Ammah wai yazo da sauri idan yana kusa. Ya Isa gidan da tunani kala-kala sai ya ɓige da samun mahaifiyar Sa’id da wasu ƴan uwanta maza uku dan dangin mahaifinsa sun rantse bazasu zo ba, ita data ɓata taje ta gyara sun dai zo na farko. Ba Smart kaɗai ba kowa ma na gidan nan yau mamakin jin maman Sa’id wai sunzo bada haƙuri ne da neman afuwar Hawwah dan ALLAH tai haƙuri ta koma yake. Smart yace shifa ƴar uwarsa bazata koma wannan gida ba, anyi kenan takardar saki kawai yake buƙata Sa’id ya kawo, dan suna sonta baza’a kashe musu yarinya ba. Sosai Maman Sa’id ke faman magiya akan wancan ma daya faru tsautsayi ne da munafuncin munafukai, amma yanzu ta gane gaskiya. Ankai ruwa rana matuƙa kafin Smart ya haƙura zata koman amma ba wannan gidan ba. Da sauri Mama tace ta yarda, Hawwah ta zaɓi duk inda take so a gidajensu a gyara mata. Wannan abu yaba kowa mamaki, Umma na son magana tana tsoron ta tanka Maman Sa’id tai mata bankaɗa tunda taji tana shaguɓe akan munafukai, ba kowa kuma ne mai zuwa ɓata Ammah da Hawwah a wajenta ba sai ita dama. Bayan wucewarsu kowa ya shiga mamaki, Abba ya tsare Smart akan miya ma maman Sa’id ɗin har tai irin wannan sakkowar lokaci ɗaya. Ya tabbatar musu bashi bane, dan shi target ɗinsa akan jiran dawowar mahaifin Sa’id ne ai. Yana son kawo Lulu a ransa wani gefe na zuciyarsa na musa masa. Amma dai duk da haka bayan ya koma gida da daddare sai da ya kasa haƙuri yay mata tambaya. Dariya kawai tayi taƙi faɗa masa komai, hakan ya tabbatar masa itace kenan tayi koma miye. Sai kawai ya zuba mata ido yana jin wani abu mai girma na ƙara ratsashi a kanta. Jin kaifin idanunsa a kanta ya sata dakatawa da ga abinda take a system ta ɗago, harararsa tai da faɗin, “Malam wannan kallon fa? Ni fa bana son kallo”. Ta ƙare maganar da murguɗa baki. Murmushi ya saki mai sanyi batare da ya janye idanun ba, sai ya samu kansa da furta, “Kullum sake mamaye komai da komai kike yi”. Bata fahimci ina ya dosa ba, sai dai yanda yay maganar a ƙasan maƙoshi da tausasa fitar sautin matuƙa ya sata tsayawa kallonsa, “Lafiya kake kuwa? Kodai kaima ka fara ban sani ba?”.
“Na fara mi?”.
“A hawa network mana”.
Ƙaramar dariya yay yana girgiza kansa. “Tom maybe na fara amma nawa ba irin naki bane gaskiya. Kema fata nake ki daina wannan ai ki dawo wannan irin nawan”.
Nan ɗin ma dai ba fahimtar tai ba, dan haka ma ta taɓe baki da miƙewa tana faɗin, “Ai kai kam wani lokacin kamar mai aljanu. Dolene na sanarma Ammah ta fara maka addu’ar su ko ka kwaso a drivern cin ba’a sani ba”. Daga haka ta wuce bedroom ta barshi yana murmushi………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣1️⃣
………Washe gari gidansu ya wuce bayan ya sauketa, anan ne yake samun Abba da Ammah da batun shifa yana zargin Mawaddat ce tayi koma miye. Dan an sanar masa taje gidan a ranar monday. Mamaki sukaitayi suma da tunanin to mita faɗa ma maman Sa’id da har ta risina haka da sauri. A gefe kuma ƙaunar yarinyar na sake shigar musu zukata. Kamar yanda akace sati ɗaya cikin satin Hawwah ta fara shirin komawa sabon gidanta danƙarere. Hankalin Umma ya sake tashi, da bin ƙwanƙwanto ta gano Lulu ce tamayi koma miye har komai ya dai-daita. Hankali a tashe ta nufi gidan Hajiya Naqiba ƙawarta. Acan suka baje faifain zagin Ammah da bata san sunayi ba da Ƴaƴanta suna neman mafita dan abubuwa fa nata faman kufce musu a hannu, sai dai gaba ɗaya hankalinsu da mugayen ƙudirinsu sun tattara ne ga Lulu yanzu. Dan sun fahimci shigowarta gidan abubuwa da yawa ke neman taɓarɓarewa. Duk da su basu fahimci cewar asirin jikin Smart ma ya gama warwarewa gaba ɗaya ba. Ga aikin Malam na-zuru yaƙi yiwuwa, dan kayan Lulu da Smart dai sun gagara ɗakkuwa. Hajiya Naqiba ce cikin dogon tunani ta ce, “Aminiya anya bazamu canja taku ba?”.
“Kamarya? Fito kimun dalla-dalla, kin san bana son kwana-kwana fa”.
“Ina nufin ba asiri bane kaɗai yanzu ya kamata musa gaba dole mu haɗa da makirci da kissa. Kamar dai yanda nai akan shegun yaran can na baƙar dagar tawa.”
“In dai wannan ne ai mun jima munayi Aminiya, yanzu ko ita akan wannan shegiyar da zata koma Hawwah ai kinga sai da muka haɗa da makirci waccan shegiyar da bamu san mitaje tayi ba ta ɓata mana komai.”
“Kwantar da hankalinki karki damu, murnarsu zata koma ciki ne. Yanzu mu fara kai wannan baƙuwar hauren ƙasa tukunna dai. Dan wannan ƴar iskar amaryar da aka jajubo muku na fahimci da ƙarfinta tazo, gashi yarinyar nada ilimi fiye da tunaninki kuma goyon turai, ga kuɗi a gida, kuɗi a mota, kuɗi a Office, kuɗi a banki. Idan mukai sake fa komai zai koma wanwarne, ni ko da kishiya da yaƴanta su ji daɗin duniya ko komawa sama dani gara ace kowa ya mutu a ƙasar, ke ama busa ƙaho”.
Dariya Umma tayi da faɗin, “Hajjaju ke bala’i ce ai, shiyyasa nake sake tausayin Matar gidan nan naki. Yanzu ke miye shawararki?”.
“Dole ne muyi bincike akan yarinyar mu samo wanda zamu shiga jikinsa nata mu mata rugu-rugu”.
“Tab babbar magana ta yaya kenan? Bayan kin san daga wane gida ta fito, gate ɗin gidan su ma taɓa shi ba masifa bane balle shiga gidan”.
“Kwantar min da hankalinki. Akwai matar nan mai min ƙunshi ranar ana labarin dukiyar da aka zubar a auren ita yarinyar da aka kai gidanku take cewa ai ita taga zahiri dan itace kema matar Alhaji Garko ƙunshi shekaru kusan shidda kenan, shiyyasa tasan abubuwa da yawa a gidan nan ko shagalin bikin nan duk akan idonsu akai komai. Ita kanta taci rabonta dan tayi ƙunshi sosai a gidan, sai dai ta fahimci kamar matar Alhaji Garko bata son auren fin ƙarfinta akayi, yarinyar da ɗan uwanta aka saka mata biki lokaci guda ta birkice wai sai yaron gidanku”.
“Kai haba da gaske wai? Anya ba asiri suka mata ba ma kuwa”.
“Wlhy haka tace, babu abinda Hafsatu bazata iyaba wlhy, wama ya sani. Shiyyasa nake ganin ya kamata muje gidan Alhaji Garko mu kunnowa Hafsatu wutar da zata ƙoneta ƙurmus har ƴaƴan nata a wannan karon. Ba suna murna sun samu ɗiyar biloniya ba. Zasuci ubansu ne”.
Dariya suka kwashe da ita suna tafawa……
_____________★★
Kwanaki sun ƙara shiɗawa, dan a lissafin Lulu dai next week ne rabuwarsu da Smart. A week ɗin daya wuce ya kaita gidansu da gidan Uncle Yousuf, daga nan ta samu ƙafar zuwa duk bayan kwana biyu haka idan ta fita aiki takan leƙasu duk da dai daga Daddy har Uncle Yousuf ɗin ma dai sunyi tafiya basa ƙasar ma. A ranta a duk sanda ta ƙiyasta tana jin farin cikin komawarta free dan ta fara jin ƙosawa da tsakurarsa musamman ta saka hijjabi da tafi cimata zuciya da rai fiye da komai. Sai dai wani sashe na zuciyar tata na mata kamar babu daɗi musamman idan ta tuna Ammah da ƴan uwansa. Takan faɗa dogon nazari akan hakan, amma idan taje duba jikin kakanta Alhaji Garko da har yanzu dai babu lafiya suna ma shirin fita da shi ƙasar ne duk da yana turjewa sai da Dada taita mata fanfo da zugeta. Wani lokacin Lulun kan nutsu ta saurareta, wani lokacin kuma tace “Kai Dada dan ALLAH wai miye matsalarki da Aliyu ne? Miyay miki?”. Dadan kan zazzageta wani lokacin ko balbaleta da faɗa dan masifaffiyar mata ce. Wannan faɗan da take takura mata da shi yasa kwana biyu Lulu bataje gidan ba, sai dai tai kira a waya taji yaya jikinsa. Hakan sai ya fara damun Dada, dan a ganinta wani asirin Smart ya sake tafkawa Lulu…
A ranar Juma’a da Lulu ke cika kwanaki uku rabonta da zuwa gidan Smart ya wuce Legos, Maryam da Asma’u aka kawo mata su tayata kwana, sai Mubarak da zaizo da dare, sai su Afrah suma da taje da kanta ta ɗebo. Nan fa shafta ta buɗe. Wucewar su Maryam ya ƙara zafar Umma, tai shiri ta nufi gidan aminiyarta Hajiya Naqiba rai ɓace. Bayan ta gama labarta mata Hajiya Naqiba tace tashi muje yau ayita ta ƙare. Sun je gidan mai ƙunshi da tace zatai musu rakkiya. Daga can suka tafi gidan Alhaji Garko. Sosai Umma ta sake girgiza da dukiyar waɗan nan mutane, nan fa zuciyarta ta ƙara ƙaimi wajen ƙulle-ƙulle na ganin auren Smart da Lulu ya gundile. Sunyi zama fin na awa ɗaya kafin hamshaƙiyar tsohuwa mai ji da kuɗi da hutu ta fito cikin isa da izzarta. Ai sai su Umma sukai saƙale suna kallon ikon ALLAH, dan Dada ta tsufa sosai kawai dai abinka da jin daɗi ne. Cikin girmamawa suka gaisheta tana amsa musu da ƙyar a yamutse. Mai ƙunshi ta mata bayani duk da dama ta fara sanar matan. Amma tsohuwar nan saita dubi su Umma a watse cike da isa ta ce, “Ku tabbatar duk abinda zai fito bakinki bazai zama wuƙar yankaku ba, dan bana son munafunci ni da kuke gani na anan”.
Muryar Umma na rawa ta ce, “Wlhy Hajiya a duk abinda mukazo miki da shi nan babu munafunci. Yaron nan asiri yayma ƴarku. Idan kuma baki yarda ba kisa malamai su bincika muku zaki fahimci gaskiyarmu. Amma kuyi da sauri dan yanzu haka yayi tafiya wai Niger da abokinsa kin san kuma yanda suka iya asiri bana raba ɗayan biyu wani bala’in zai sake haɗo muku (😂 Niger akacema su Umma Smart ya tafi raka Ahmad sayen shanu).
Mai ƙunshi da yake itama makirar mace ce tana kuma son sake samun fada a wajen Hajiya Dada sai ta sake taƙarƙarewa tana taya su Umma. Harda cewa zata raka Dada wajen wani malami a duba musu ɗan uwanta ne a Zuru yake. Amma batai maganar hakan ba sai da su Umma suka fito bayan an sallamesu. Hankalin Dada ya tashi, dan haka ta sallami su Umma tace mai ƙunshi tazo ta sameta gobe idan ALLAH ya kaimu bayan an wuce da Alhaji Garko dan zasuyi gaba ƙasar London ita sai nan da sati ɗaya zatabi bayansu. Cike da farin ciki su Umma suka fito da ƙyautar naira dubu ɗari kowa hansin-hansin. Mai ƙunshi kuwa ma basu san mi aka bata ba. Ta kumace dole su cire mata kasonta a ciki dan bazata rakosu a banza ba. Da ƙyar suka bata goma-goma suna ƙunƙuni. Tace oho dai shegu ai ni kunzo min da hanyar samun kuɗi, naci a wajenku, naci a wajenta, naci a wajen malamin da kukace aje.
Washe garin asabar aka wuce da Alhaji Sufi Garko ƙasar London dan likitoci anan gida Nigeria sun tabbatar poising ɗinsa akayi. Ba’a fahimci hakan ba kuma sai a tsakanin kwana biyun nan da gubar ta bayyana kanta, dan sun bashi wadda bata bayyana kanta da wuri har sai tayima jiki illa ne. Duk da wannan tashin hankalin da ake ciki hankalin Dada nakan Lulu da itama dai yau tazo gidan har da su Asma’u da su Afrah. Sai dai taƙi yarda ko sau ɗaya su zauna da Dada har sanda ambulance ta ɗauki Baba itama sai taja ƴan rakkiyarta suka bisu har airport. Basu baro ba sai da jirgin da za’a ɗauke sa a ciki shi kaɗai sai yaransa maza biyu ƙannen Alh Sulaiman da zasuyi gaba ya tashi. Kowa ya bisu da addu’a kafin yaje. Suna baro airport ɗin jirgin da ya ɗakko Tajuddeen da Alhaji Sulaiman (Tsule🤣) ya sauka shi kuma. Ya samu sauƙi sosai koma muce a zahiri ya warke, sai dai a zuciya kam babu abinda ya ragu na soyayyar da yakema Lulu. Ya samu kwanciyar hankali da nutsuwar zuciyane kawai bisa alƙawarin da mahaifinsa yay masa na sai ya mallaka masa Mawaddat ya kwantar da hankalinsa. Wannan dalili ne ya sashi jin ƙwarin gwiwar biyosa suka dawo. Manyan aminansa na yanzu duk da dama can aminan nasa ne matsaloli suka rabasu Alhaji Baita, Hon. Nakowa. Da Hon. Misau ne sukaje tarbarsu. Dan kaf Family na Garko babu wanda yasan da dawowar tasu a yau…….✍️
(🤔Tofa! Alhaji Sufi Garko ya tafi jiyya a dalilin poising nashi da akace anyi. Alhaji Sulaiman Sufi Garko ya dawo tare da ɗansa Tajuddeen Sulaiman Sufi Garko daya tashi a jiyyar soyayya babu wani damuwa tattare da al’amarin su. Anya kuwa babu wani abu a ƙasa? Humm kumu dai je zuwa to🚴).
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣2️⃣
…….Dada tayi tunanin Lulu zata sake dawowa gidan, amma bayan duk ƴan rakkiyar Baba sun dawo sai gashi babu ita, sai ma sanar mata da akai ta wuce gidan ta. Hakan ya sake girgiza Dada ta kuma tabbatar da eh lallai da alamar ƙamshin gaskiya a zancen mutanen nan asiri yaron nan yay ma jikarta. A take ta dannama Fulera mai ƙunshi kira, batare dako amsa gaisuwar ta ba tace ta sameta yanzun. Fulera ido a kuɗi tuni tai tsalle tayo waje da ga gidan su, dan dama dai zawarci take kusan shekara tara kenan. Cikin ƙanƙanin lokaci sai gata a Garko house. Ta sami Hajiya Dada tare da mai aikinta dake mata irin waɗan nan ayyukan na sirri, dan Dada tunda jajayen sawu ƴan hannun bin malamai ne kam. Cikin gurfana Fulera ta miƙa gaisuwa, Dada ta amsa cike da isa. Babu wani jan lokaci ta sanar musu abinda take son a mata. Zasuje wajen mutumin da tace mata a Zuru ita da mai aikinta. Ba haka Fulera taso ba, amma dai babu damar musu dan haka ta amsa da to. Mota Dada ta bada akaisu tare da kuɗin amma sai ta damƙawa mai aikin nata. Nan ma Fulera taji zafi, ta dai danne, damar fara fita data samu kafin mai aikin Dada ta kimtso ta samu ta dannama Hajiya Naqiba kira ta sanar mata komai. Dariya Hajiya Naqiba tai da faɗin, “Kai tsohuwar nan mayyace akwai shegen wayo. Barta ai inta san wata bata san wata ba. Kwantar da hankalinki bari na kirashi kafin ku isa.”
Haka kuwa akai hajiya Naqiba tai kiran malam na-zuru, duk yanda suke so haka ta tsara masa, shima da yake shegen kansa ne yace karta damu. Abinka da lafiyayyar mota basu sha wahala ba, dan bayan azhar kaɗan suka isa zuru saboda gudu na masifa da drivern yayi. Malam na-zuru da yake yasan da zuwansu kafin ma su faɗi abinda ya kawosu ya shiga zayyane musu wai ai ya gani ne a cikin aikinsa. Tuni mai aikin Dada ta ruɗe ta danna mata kira, nan ma fa sukai magana da malam Na-zuru ya sake fanfa Dada da kalolin sharri wa Smart dangane da auren Lulu, harda cewa ai asiri Smart ɗin yay musu dan yaga kuɗi. A yanzu haka ma yana Niger yaje anyo masa wani babban ƙulli, zaita kwantar musu da kai ya nuna shi na ALLAH ne sai anan gaba kaɗan zai bayyana halayyarsa da mugun nufinsa. Tsaf Dada tahau ta zauna saboda tayi imani da malaman tsubbu matuƙa gaya. Malam na-zuru ya haɗa musu kayayyaki suka sake ɗakko hanya….
WASHE GARIN Lahadi Lulu da ƴan kwananta ta zubasu a mota ta kaisu sabon Saloon da ta fara zuwa yanzu ana mata gyaran jiki. Tsaf aka gyara ƴammatan nan suka fito tas da su kamar basu ba. Daga Saloon sun shiga wani joint suka ɗan sha ice-cream da abinda baza’a rasa ba. Daga nan suka koma gida. Kasancewar duk sun gaji kuma basa tare da yunwa suka shige ɗakin dake matsayin masaukinsu masu kwanciya nayi masu fira nayi. Itama anan falo ta ɗan kwanta dan ta haɗiyi kayan nata duk da kaɗan take sha dan kar yaran su fahimta. Wayarta ce ta shiga ruri, takai hannu ta ɗauka tana jan ƙaramin tsaki. Ganin Dada ya sata waro idanu waje, sai kuma ta ɗaga da sauri. Kafin tace komai Dada ta ce, “Ina mai gadin naku anata horn kamar ya mutu”. Da mamaki Lulu tace, “Mai gadi kuma Dada? A ina wai?”.
“Gidan da aka kawoki mai kama da bukkar fulani”.
Dariya Lulu tai tana miƙewa. Ta ce, “Uhm Dada baƙya gajiya dama mutane sharri idan baki son su. Wannan gidan ko makaho ya shafa ai yasan badaga nan ba. Ina zuwa”. Ta yanke wayar tare da zura slippers ta fita. Da kanta ta buɗe musu gate ɗin. Dada na hakimce a bayan danƙarereiyar motar da sukazo baƙa wulik, sai drivern ta. Koda ya samu waje yay parking sai da ya buɗe mata ta fito tana wani yamutse fuskartar ta tsufa da bin gidan da kallon banza. Yi Lulu tai kamar bata fahimceta ba ta rungumeta tana murnar ganinta. Dada ta tureta da faɗin, “Ni karki kadani fitinanniya”.
“Ni na isa kadaki Hajiyar Baba Garko. Yanzu yana asibiti yana fama da kansa ke kina nan kina yawo”.
“Oh kijimin yarinya da ƙulli, yanzu zuwa na dubakin kuma bammayi miki gwaninta ba kenan”.
“A’a kimun yi haƙuri muje ciki”.
A falon ma dai Dada sai yamutse-yamutse take duk da ya mata ƙyau matuƙa. Nan ma Lulu tai kamar bata lura ba taje ta kawo mata ruwa da lemo. Tana zama ta jeho mata tambayar “Ina yaran dana ganki da su ɗazun?”. Cikin rashin damuwa Lulu ta nuna ɗakin da su Maryam suke. Ɗan jimm Dadan tai sai kuma ta miƙe, “Kinga muje ɗakin ki magana nazo muyi”. Babu musu Lulu ta miƙe suka nufi bedroom ɗinta da Asma’u ta gyara ƙal sai tashin uban ƙamshi yake yi. Nan ma dai sai da Dada ta gama ƙare masa kallo sannan ta ja numfashi. “Kaya har kaya anzo an zubesu a wannan takurarren gidan.” ƙin cewa komai Lulu tayi, dan haka Dadan ta cigaba da faɗin, “Game da zuwa duba Alhaji ne. Shin zakije ne?”. Ɗan jimm Lulu tayi, sai kuma ta nisa da faɗin, “Ina son naje kam Dada, sai dai yanzu Aliyu yayi tafiya maybe ya dawo gobe. Idan ya dawo mukai magana sai kiji”. Sosai zantukan lulun ke sukar Dada da sake gaskata fa amma jikarta asiri, yo Mawaddat ɗin ta data sani mai zafin nan da ƙyamar abu ga murɗaɗɗen hali wai namiji ke juyawa haka. Namijin ma talaka ɗan talakawa fitik mai amsa sunan drivern ta. Kai wannan al’amari akwai ayar tambaya. A zahiri kam murmushi tai da cewa, “To ba laifi hakan ma yayi. Af kinga zan manta ga wannan kisha maganin ciwon maran nan ne dake damunki dama nace zan amso miki, inata shiririta sai kwanaki aka amso kinata zuwa gidan kuma ina mantawa. Shiru Lulu tayi tana kallon goran ruwan kamar tace a’a sai kuma dai ta amsa, dan ranta bazai taɓa bata Dada acikin jerin wanda zasu iya mata wani abu daban ba, sannan tana saran ganin period ɗinta nan da kwana uku, tasan kuma azabar da take sha na ciwon maran. Amsa tai ta ajiye gefe, amma sai Dadan tace tasha mana. Ai ba’a wasa da magani. Badan Lulu taso ba ta buɗe tasha kusan rabi ta ajiye. Daga haka suka cigaba da hirarsu da Dada wadda duk bugun cikine akan auren nan da son sanin wanene Smart. Ita dai Lulu tana bata amsar abinda ta sani ne kawai, har cikin ranta kuma bata kawo komai ba. Sai da Dada take cemata tafa kula, karta yarda yaron nan ya mata wayo ya kwanta da ita, dan yanda kwanakin nan suka kusa cika zai iya shirya mata muguntar maza. Lulu tai murmushi da faɗin, “Dada kenan nace miki ki kwantar da hankalinki, Shifa Aliyu ba irin waɗan nan da kike tunani bane. Na tabbata tunda har ya amince da auren nan na wata ɗaya ne kuma zai sake ni bazai taɓa saɓawa ba zai sake nin, yanzu haka ma jiran dawowarsa nake mu fara maganar dan shiyyasa nace ki dakata da batun tafiyar nan, cases ɗin dake gabana zanyi ƙoƙarin kammalasu na ɗan ɗauki hutu daga duba Grandpa zan ɗan huta kafin na dawo Nigeria gaskiya”.
Sosai Dada taji daɗi dan haka ta shiga sanya mata albarka. Daga haka ma sai ta miƙe tana faɗin, “To bara na wuce tunda na kammala abinda ya kawo ni. Sai na jiki ɗin”.
Da sauri yabar jikin ƙofar ya shige bedroom ɗinsa. Wani irin harbawa zuciyarsa keyi da sauri-sauri. Dan shigarsu ɗakin babu jimawa ya shigo gidan. Duk da yay mamakin ganin mota baƙuwa a waje yay zaton kota Lulu ce aka kawo saboda bai ga driver ba, ashe ya ɗan fita miƙe ƙafa. Ya shigo gidan yaji shiru, ya wuce ɗakinsa kai tsaye ya ajiye kayan hannunsa shine ya nufo ɗakin Lulu da tunanin ko barci take. Kawai yaji Dada na magana a hanakali cikin salon makirci na tsoffin mata tana bugar cikin Lulu, shine fa ya nutsu. Jin komai ya sake tada masa da hankali, dan yanzu ne ya fahimci ainahin abinda take nufi da wata ɗaya wata ɗaya da take ta ambata masa zata koma free. Zuciyarsa ta sosu da tunanin shima Uncle Yousuf yaudararsa yake kenan? Sai kuma wata ke kwaɓarsa akan kada yay zargi cikin fushi, ya bincika dai sannan. Sunayen ALLAH ya shiga ambata har ya samu nutsuwar ajiye tunanin a ransa gefe, sai kawai ya faɗa wanka. Lokacin da yake fitowa yaji fitar motar data kawo Dada, sai kawai ya ƙarasa kimtsawa da yin shirin fita sallar magrib ya fito.
Lulu da ke kwance a falo ta wani ɗan zabura alamar tsorata da ganinsa. Murmushi ya sakar mata da lumshe idanu yana kaiwa zaune kusa da ƙafafunta. “Matsoraciya relax ba aljani bane ni ne?”.
“Taya zan yarda da haka bayan kace sai gobe ne zaka dawo, kuma ina wajen banga sanda ka shigo ba”.
Murmushin ya sake sakar mata, a nutsensa da deep voice ɗin nan tasa dake fita da sanyin damuwar abinda yaji na tattaunawar ta da Dada duk da yana ƙoƙarin dannewa ya ce, “Mun gama abinda ya kaimu ne shine kawai muka yanke dawowa gida. Sanda na shigo kuma kina ɗaki ne da baƙuwa. Namayi zaton har zan kammala wanka nazo mu gaisa duk da bansan wacece ba”.
Kaɗan ta sauke numfashi da ɗage kafaɗunta. “Dada ce kuma ta wuce. Tazo ne akan maganar zuwa duba Grandpa da aka wuce da shi London jiya”.
“Ya salam jikin nasa ne dai?”.
“Wlhy kuwa, fiye ma da yanda ake tsammani, dan a shekaran jiya doctors suka gano wai anyi poising ɗinsa ne da gubar da bata baiyana kanta sai tai kwanaki a jikin mutum”.
“What! Sai kace wani a film?”.
Lulu ta ce, “Hummm a tunaninka a Film kawai ake waɗan nan abubuwan? To a Nigeria ma a zahiri anayin fiye da haka. Kasan Grandpa ya Bama siyasar nan amanna matuƙa, shiyyasa muke tunanin ko’a cikinsu ne musamman daya kasance a hasashenmu a zuwa Legos ɗin nan da yay abun ya faru. Yanzu dai haka jami’an tsaro sun duƙufa bincike kan al’amarin ma”.
Matuƙa Smart ya girgiza. Dan baiyi zato ko tsammanin wai da gaske irin wannan abubuwan da ake gani a Film na faruwa a zahirin rayuwar mutanen ƙasarsa ba. Kiran salla ta sashi miƙewa yana faɗin, “Ina ƴan hutun naki? Naji gidan shiru”. Bedroom ɗin da suke ta nuna masa. “Suna ciki fa, tunda muka dawo saloon suka kwanta wai sun gaji”. Kallonta ya tsayayi kamar zai yi magana sai kuma yay shiru dan shi dai bai san da wani fitarsu saloon ba. Zuciyarsa ta lallashesa akan a tari gaba. Yanzu zantukan ta da Dada ya kamata ya maidama hankali. Kafaɗa ya ɗan ɗage hannayensa duka a aljihu, ya ce, “Okay bari naje salla na dawo. A ɗan samamin wani abu mai ruwa-ruwa haka yunwa nake ji”.
Harararsa tai da faɗin, “Kafa dawo zaka fara takurama mutane da mulkinka ko”.
“Ni na isa. Karki damu cikin su Maryam wani yayi ki huta abinki. Ki dai tashi kiyi salla. Bara naje sai na dawo”. Daga haka ya fice kafin ma tace wani abu……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣3️⃣
……..Bayan an idar da salla har ya nufo hanyar gidan sai kuma ya dakata. Napep ya tare ya shiga tare da gaya masa inda zai kaisa. Cikin ka ƙanƙanin lokaci suka iso. Ya biya sa kudinsa sannan ya shiga gidan bayan sun gaisa da maigadi. Ahmad na zaune a falonsa ya barbaza takardu ga laptop a gabansa Smart ya shigo. Ɗagowa yay yana kallonsa cikin nuna mamaki. Smart ya watsa masa harara da faɗin, “Lafiya kake kallona?”.
“Inafa lafiya, kai da nake tunanin kana can kana aikin ALLAH yanzu kodan kewar juna da akai amma sai na ganka anan”.
Ƙaramin tsaki Smart yay yana kaiwa zaune da faɗin, “Banza ɗan iska kaifa baka tauna magana kafin ta fito maka a baki”.
Dariya Ahmad yayi da cewa, “Gara na dinga muku ɓaro-ɓaro kuyi ku aurar dani kuma ku huta. Amma fa sai naga kamar kana cikin damuwa. ALLAH dai yasa ba wani abu ka tarar a gidan ba?”.
Smart baida yawan magana. Sannan akwai zurfin ciki. Duk abinda kaga ya bayyana shi ga waninsa to lallai ya matuƙar girgiza shi ne. Sosai ya nisa da furzar da iska mai zafi. “Ahmad akwai matsala ne”.
“Ya salam matsala kuma Mawashin. To tami? Akan kuma mi?”.
Shiru kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya ɗago yana kallon Ahamd ɗin da shima ya zuba masa idanu. “Badan ina son fara tona sirrin gidana bane, al’amarin ya girgiza nine ina buƙatar shawara dan kar na aikata abinda ba haka yake ba. Bayan kun saukeni na shiga gida sai na samu…….”
Tsaf ya zayyane masa abinda yaji tsakanin Lulu da Dada na tattaunawa. Shima kansa Ahmad yasha mamaki. Amma sai ya dafa Smart yana jinjina kansa. “Niko kaga ko bana jin shi Yaya Yousuf da wata manufa yay hakan. Domin idan ka auna zancen tsohuwar zaginsa take akai-kaice shima. Sai naga yayine domin ma Mawaddat wayo kawai”.
“To miye na wayon anan Ahmad, aure ne fa kuma ta isa aure tunda ba gunkinta zasuyi su kafe a gidan ba. Kawai dai akwai abinda suke shiryawa a kaina na yaudara”.
“No no relax kar kabari ka yarda da hakan. Sam sam bazaiyi hakan ba. Amma ina zuwa dai”. Waya Ahmad ya ɗakko yay kiran Uncle Yousuf. Da ƙyar ya samu ya shiga kasancewar har yanzu bai dawo ƙasar ba. Sun gaisa cikin mutunta juna batare daya nuna yana tare da Smart ba. Uncle Yousuf daga can cikin tsokana yace, “Yaya dai Auta ko batun auren ne ya tashi akeso na fara haɗo lefe?”.
Dariya Ahmad yayi da faɗin, “Kai haba Yaya a’a. Wannan ai sai kun yarda da zaɓina sannan zamuje wannan matakin. Duk da nasan ma kunaji da gudu zaku amince. Wani abu ne fa da na jiyo ya girgizani. Sai nace bari dai na kiraka ko kasan da zancen”.
“Oh to Masha ALLAH, ALLAH ya tabbatar da khairan sa. Minene kake son ji haka?”.
“Uhm wlhy Yaya nafaje gidan Smart ne ɗazun sai na samu Mawaddat na waya cewar ai ta kusa komawa free nan da 4days aurenta zai ƙare da Aliyu. Abin ya girgizani matuƙa”.
“Ya Arrahaman”. Uncle Yousuf ya faɗa daga can cikin dafe kai. “Yaya kama sani kenan?”. Numfashi Uncle Yousuf yaja da saukewa. Sannan cikin nutsuwa ya sanarma Ahmad yanda akai zancen ya fito, ya ɗora da faɗin, “Ni ko ma Aliyun bamma maganar ba dan ba haka bane a raina. Wannan auren ina fatan sai mutuwa ce zata rabashi. Na saki jiki ne da tunanin tana zuwa gidansa zaibi duk hanyar daya dace wajen mantar da ita wannan shirmen. To ashe wata sabuwa ita hakan na ranta. Dole ne na kira Aliyu na sanar masa komai sannan kuma ya ɗauki duk ma matakin daya dace akan hakan. Amma zanyi ƙoƙarin dawowa nima duk da ban gama abinda nake ba. Dan ALLAH kaima ina son ka zaunar da Aliyu ka nuna masa abinda ya dace akan wannan batun. Idan ma yana ma Mawaddat saku-saku ne ya ajiye gefe ya koma wuta-wuta tasan shi bamu bane ba. Idan komai ya daidaita ya mata sauƙin”.
“Shike nan Yaya insha ALLAHU yanda mukai da shi zakaji”. Daga haka ya yanke kiran. Smart yaji komai dan a hansfree yasa baya buƙatar ƙarin bayani, sai ma ajiyar zuciya da ya sauke dan ya fahimci Uncle Yousuf ɗin da manufarsa akan hakan. Ya kuma daina ganin laifinsa dan ko shine abinda zai yi kenan domin toshe kowace matsala da zata iya ta taso a lokacin…. Ahmad ne ya katse masa tunani da faɗin, “Mawashi a yanzu fa wannan yaƙin naka ne bana wani ba. Kai ya kamata ka nuna mazantaka komai ma za’ayi ayi karka biye mata. Sannan na fahimci kamar ido ka kawo ka zubamata shiyyasa ma take ganin komai normal ne. Dole fa kai ƙoƙarin dashen shukarka dan hana kowace irin barazana tasiri. Dan hatta da ita kanta hakan da zakai zai karya lagonta dan bazata taɓa yarda a tunɓuke wannan shukarba”.
Tsaf Smart ya fahimcesa dan haka yay ɗan gajeren murmushi yana girgiza kai. “Ahmad bazaka fahimta ba. Mawaddat fa ta wuce duk yanda kake tunani. Sannan ni harga ALLAH bana son zuwa gareta batare da amincewarta ba. Shiyyasa na sake mata tare da nuna mata har yanzun a ƙasan nata nake dan hakan ne kawai zai iya karya lagonta harta saki jiki dani. Kuma Alhmdllh naga hakan yana tasiri sosai akanta . Taya kake tunanin yanzu na tunkareta da wannan sigar ai babu zaman lafiya”.
“Humm kaifa na manta ashe sunanka namiji ɗaya tilo a tsakkiyar ƴaƴa mata shiyyasa. Mawashi na yarda da yanda ka tsara ɗin kuma hakan ma hanyar maslaha ce mai ƙyau da anan gaba ita kanta sai tayi alfahari da kai. Amma kai ya kamata ka memo hanyar da zakabi ta amince maka da kan nata ku zama ɗayan. Mudai fatan mu ai ayi shukar dan shi kaɗaine nake ganin zai hanata kowane irin motsi musamman daya kasance a yanzu tanada defenders a gefe kuma masu ƙarfi.”
“Na yarda da kai, amma kuma tayaya zanyi hakan batare dana ɓata abinda na fara ginawa a zamanmu ba?”.
Dariya sosai Ahmad ya shigayi har sai da Smart ya fara ƙuluwa sannan ya sassauta. Ya ce, “Shiyyasa nace kaifa gata yay maka yawa na kasancewarka ɗa namiji ɗaya tilo a tsakkiyar mata shiyyasa abubuwa da yawa kai hoto ne. Karka damu wannan aikina ne. Kai dai yanzu tashi ka koma gida ka maida komai ba komai ba. Amma yaran nan data cika gida da su ka tattarasu gobe su koma gida”.
Cikin ɗan taɓe baki Smart yace, “Dama zasu koma goben ne ai saboda school. Amma ka faɗamin mi zakayi?”
“Babu ruwanka da abinda zanyi, ai kasan dai bazan cutar da kai ba.”
“Na sani, amma dai ya kamata ace na sani ko”.
“Karka damu zaka sani, nima sai nayi mazari”
Daga haka suka fito anan massalacin ƙofar gidan su Ahamd sukai salla. Ya amshi key ɗin motar Ahmad ya wuce gida. Yanzu kam ya samesu su duka a falo suna kallo. Sannu da zuwa suka shiga masa a zatonsu isowar kenan. Ya zauna yana amsa musu da tambayar lafiyarsu. Lulu na zaune a ƙasa tana shan fruits da aka yayyanka a bowl. Ta sauya kaya alamar wanka tayi, dan wando ne da riga marasa nauyi a jikinta. Kan babu ɗan kwali ya dai sha gyaran da sukayo yau sai ƙyalli yake yi. Idanunsa ya ɗan lumshe da sake lafewa cikin kujerar zantukan Ahmad na dawo masa a rai dalla-dalla. Shi yasan akwai ƙura, dan ko za’a kaisa jail sakinta bazai taɓayi ba koda a mafarki ne. Maryam ce data kawo masa abinda yace a masa cikin hikima ta janye su Amrah suka koma ɗaki tunda acan ma akwai tv. Lulu ta bisu da kallo tana faɗin, “Ku kuma ina zaku muna hira?”. Da dariya Maryam tace, “Aunty muna zuwa sirri zamuyi mu dawo yanzun”.
“To ALLAH dai yasa bani za’a ƙullawa ba”.
Dariya suka shige sunayi, yayinda Smart ya sakko ya zauna a ƙasan kusa da ita. Hannunta ya riƙo ya kai apple ɗin data ciro jikin cokalin bakinsa. Juyowa tai ta hararesa. Yay murmushi da ɗan kashe mata ido ɗaya. “Idan ma ke zasu ƙullawa ba gani a kusa da ke ba sai na kunceki tsaf na maida igiyar kansu Madam”.
“A’a Granny ƙarewar Madam”. Ta faɗa tana sake balla masa harara. Dariya yayi yanzu kam fararen haƙoransa na bayyana da ƙyau. Sai da taji wani zuuu cikin kanta amma tai azamar ɗauke idanun cikin basarwa. Shiko ya cigaba da faɗin, “Ai ki godema ALLAH da baki zo a kakar tawa ba. Gaskiya da Kinga takanki dan sai na addabeki”.
“Sai dai ko mu addabi juna. Dan kaima kasan Lulu ƙamshi ba kanwar lasa bace.”
“Niko nasan haka”.
Ya faɗa cikin ɗage gira. Kankanar data tsiro ta tura masa a baki tana harararsa. Ya shiga shan abarsa yana murmushi. Itako ta maida hankalinta a kallon da sukeyi dan tana matuƙar son film ɗin duk da horro ne. Shima gyara zamansa yayi ya matsa jikinta sosai ya jingina bayansa da kujera kamar yanda tayi. “Wai sai sha kike baƙya bani ALLAH sarki autan Ammah akwai haƙuri”. Ya faɗa a mararairaice. Juyowa tai ta kallesa, sai kuma ta kalla fruits ɗin. “Oh kace kwaɗayi ya zaunar dakai nan ɗin ba kallo ba ashe?”.
“To kusan haka”.
Ya bata amsa yana shafar sumar kansa da bata da yawa can sosai, sannan tafi saisaye kuma. “Kwaɗayi dai mabuɗin wahala ne” ta faɗa tana tsiro abarba ta miƙa masa. Maimakon ya amsa cokalin sai ya riƙe hanunta ya kai abarbar bakinsa a haka da nata hannun. Batace komai ba ta janye hanunta daga nasan. Sai ta koma idan ta sha saita tsira ta miƙa masan, shi kuma ya riƙe hannun nata ya kai bakinsa. Harda ɗan kwanto kansa a kafaɗarta kaɗan. Shagala datai a kallon yasa bata maida hankali ba duk da tabbas tana jin kan nasa a kafaɗarta sai dai ba sakar mata nauyi yay ba sosai.
“Wai ko ki tambaya inda naje, da zan tafi baki tambaya ba. Ina can munyi waya baki tambaya ba. Na dawo ma haka. Anya zaman tare yace haka Mawaddatan’warahmah”.
Yanda ya kirayi sunan nata sai da taji zuciyarta ta motsa. Duk da kuwa Uncle Yousuf kan kirata da sunan lokaci zuwa lokaci. Kansa da ke a kafaɗarta ta ture da faɗin, “Mi haɗina da tafiyarka da dole zan dage sai naji. Ko salan a kirani mai gulma kuma”.
“Haka ne kuma fa”.
Ya bata amsa cikin rashin damuwa. Sai kuma ya jawo tray ɗin da Maryam ta ajiye ya buɗe ƙaramin flaks da ta saka kunun madara a ciki ya zuba a cup, kaɗan yasa suga. Ya fara sha ya lura tana kallonsa. Kofin ya miƙa mata batare da yayi magana ba. Sai ta ɗan yamutsa fuska tana girgiza kanta.
“Da akwai daɗi fa, ɗan-ɗana kaɗan kiji”.
Kamar bazata amsa ba sai kuma dai ta amsa ɗin, kaɗan ta ɗibo a spoon ɗin takai baki. Sai ta ƙara ɗibowa tana kallonsa. “Akwai fa daɗi, ni dana ga tanata haɗa-haɗa sai na ɗauka jagwalgwali ne kawai”.
Murmushi yay mata da amshe spoon ɗin yana faɗin, “Karkuma ki shanye min to daga tayi”.
“Oh ashe ba daɗi ni ka shanye mun fruits ɗina.”
“Tofa gori ne abun? To shikenan musha”. Ya faɗa yana miƙa mata. Amsa tai ta sha ta miƙa masa itama, haka suka dingayi yanzun ma dai da spoon ɗaya suna kallo. Ya ƙare ya sake ƙara musu wani. Sai gashi sun shanye kunun flaks ɗin duka. Farfesun dake cikin kwanon kuma bai ciyu ba. Suna a falon har sai da Film ɗin ya ƙare. Shi ya kwashe kayan ya kai kitchen tare da kashe komai ya rufe ƙofar. Ita kuma ta tattara kayanta ta wuce ɗakinta ko sai da safe babu. Da kallo kawai ya bita yana girgiza kai, shima sai ya nufi nasa ɗakin. Sai da ya kammala komai na al’adarsa kafin kwanciya sannan ya canja kayansa zuwa na barci yasa turare yay brush ya fice. Lulu na zaune a tsakkiyar gadonta tana aiki a system ya shigo. Kallonsa take da mamaki daga sama har ƙasa. Kafin cikin ƙarfin hali ta ce, “Lafiya kuwa?”.
“Ƙalau”.
Ya faɗa a taƙaice yana hayewa gadon…….✍️
😜Wace gulma ta kawoshi ka to🚴
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣4️⃣
…….Sai da ya kai kwance duk tana kallonsa sannan ya cigaba da faɗin, “Zan kwana anan dan karma yaran can su fahimci wani abu daban har su faɗa a gida. Bazan so Ammah taji abinda bashi take fata ba a rayuwar gidana”.
Duk da maganar tasa ta ɗan zabureta a zuciya sai ta kanne da tureta gefe ta ɗauke kanta. Sai kuma ta juyo da tura masa bargo ta ce, “To ga duvet nan koma sofa. Dan wlhy ban iya kwana da mutum biyu a gado ba, a cikin ɗaki ma kowa da makwancinsa ko yara ne takura nakeyi. Balle ma kai ƙato da kai ai saika sakani firgita”.
Dariya maganar tata ta bashi, amma sai ya kanne baiyi ba yay ɗan murmushi kawai da kai hannunsa kan tarin fillos dake a gadon ya jawosu. Ita ya kalla da faɗin, “Kinga ɗan matsa gaba”. Matsawar tai shi kuma ya shiga jera fillos ɗin a tsakkiyarsu. “Gashi nan nikam an raba basai kin korani saman sofa ba dan bazan iya barci acan ba nima.”
Harararsa tai da sake faɗin, “To nifa wlhy zan iya tsorata?”.
“Saboda mi? Bayan kin san dai ni ne kuma bazan kawo wani hari ba inma yaƙin ƙasa da ƙasa kike tsoro”.
Ba fahimtarsa tai ba ita kam. Dan haka kai tsaye ta ce, “Kawai dai bana son namiji kusa dani, dan yana tuna min abinda bana son na tuna?”.
(Anzo wajen) ya faɗa a zuciyarsa. A zahiri kam sai yace, “Ai komai nada dalili. Miyasa hakan?”.
“Humm manta kawai”.
Ta bashi amsa tana maida hankali ga laptop ɗin tata. Shiru yay dan baya son nuna mata zaƙuwarsa na son ji. Sai ma ya lumshe idanunsa kamar wanda yay barci. Itama aikin ta cigaba da yi zuciyarta dai na wasuwasi akan kwanansa a ɗakin, wata kuma na ƙoƙarin nusar da ita na yau ne ai kawai. Bashi da wata manufa kuma tunda bai taɓa gwada makamancin hakan ba sai yau da yaran nan ke a gidan. Haka dai ta cigaba da saƙawarta da kwancewa har aikin ya nema gagararta, da ga ƙarshe dole ta kashe system ɗin da tattare takardun data baza. Juyawa tai tana kallon Smart da ke sauke numfashi a hankali, da gaske yanzu kam yayi barci dan a gajiye yake matuƙa. Sai ta samu kanta da sauke numfashi mai nauyi itama. Sauka tai a gadon ta nufi bayi, bata jima sosai ba ta dawo. Kasancewar dama wutar ɗakin ba wata mai haske bace can sosai ya sata ɗan tsayawa tana kallonsa da alama dai har yanzu zuciyarta na rawa, dan kallon da take masa bawai kallone irin na ka ɗauki hankalina ba, a’a kallone irin na nazari akan son yanke hukuncin na yarda ko kar na yarda?. Ta jima a wajen tsaye har ƙafafunta suka fara mata dayi sannan ta jasu da ƙyar ta koma saman gadon dai ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya a jere. Addu’ar barci da yakan gargaɗeta ta dinga yi wanda Alhmdllh ta yi nisa kaɗan a koyansu ta fara, sai dai bata zaton takai ko rabi ba barci ya kwasheta. Dan itama ɗin dai akwai gajiya tattare da ita, sannan da rana bayan dawowarsu ta sha syrup kwalba ɗaya. Gaba ɗayansu kamar wasa duk sai barcin yay musu nauyi sosai, kusan gabannin asuba Smart ya farka, jin abu a jikinsa da ɗumin da baiyi kama dana bargo ba ya sashi buɗe idanunsa da ke cike da nauyin barci da ƙyar. Akan ƙyaƙyƙyawar fuskarta ya sauke cikin ɗan hasken ɗakin, barcinta take hankali kwance lafe a jikinsa kamar wata ƴar mage. Sai da ya ɗan waro ido na mamakin yaya akai hakan ya faru? Juyawa yay ya kallesu su da gadon, sai yaga tabbas shine ya ture filos ɗin tsakkiyarsu da ya jera ya dawo inda take. (Ɗan Ammah kaika fara kawo wannan harin na tsakanin ƙasa-da-ƙasa fa kenan) ya ayyana a zuciyarsa. Sai ya samu kansa da sakin murmushi yay ɗan luuu da idanu yana maida kansa ga filonta da ya dawo kai. Kamata yay ace ya koma inda yaken kafin ta farka dan kuwa dai yasan zai sha cara, to amma yana yin wani motsi fa zata iya farkawa matsalar da yake gudun ta afku saboda a jikinsa take sosai, sai kawai ya zaɓi zubama sarautar ALLAH ido tunda akwai sauran daren, shima sabo da tashi yin nafilfilin daren ne ya sashi farkawar. Gashinta da duk ya zazzame da ga cikin ribbon da aka ɗauresa yasa hannu ya gyara mata, sai ƙyaƙyƙyawar fuskar tata ta sake fitowa fes da ƙyau. Kwanciyarta tai ƙoƙarin gyarawa da sake mamuƙesa a cikin barci batare data sani ba, dan ta kasance mai ɗabi’ar rungume filos idan tana barci, a yanzun ma dai da alama hakan take tunanin tayi, batasan baban filos bane gaba ɗaya😂. Ba shiri Smart ya rumtse idanun da ƙarfi yana cije lips, (Wayyo ɗan Ammah itamafa ta kawo hari wlhy, shike nan ƴan tada zaune tsaye sun fara tattaro makamai) ya sake faɗa a zuciyarsa yana matse jikinsa a waje guda sai dai ina a jikin nasa take ma gaba ɗaya, ta kuma cigaba da barcinta hankali kwance. Wata wawuyar ajiyar zuciya ya sauke da buɗe idanun da ƙyar a kanta. Wannan fa shi ake kira siye da kuɗi yafi siye da bashi, dan fuskarta ta sake matsowa kusa da tashi sosai ga numfashinta da ke sauka masa a kan fuska na sake rikita masa lissafi. Maida idanun kawai yay ya rumtse, sai dai zuciyarsa da gangar jikinsa sunki yarda da wannan lallashin, har takai baima gama yanke hukuncin abinyi ba kawai ya sauke lips ɗinsa akan nata, tun yanayi cikin shakka-shakkar karta farka har ya dake kawai abinsa yama ɗaura hannunsa sosai a jikinta ya sake turata ciki. Sam Lulu bata da nauyin barci, dan haka ta farka kuwa jin baƙon al’amari a gareta, sai dai nauyin da idanunta sukai da ma jikin nata ya sata jan sakanni kafin ta fahimci mike faruwa. Wannan ma wata dama ce ga Smart dake shagulgulansa batare da yasan ƙasar da ya kaima harin ta farka ba. Lokacin da ya kamata ta ɗauki mataki itama jikin nata ya fara amsar harin nasa, sai ta samu kanta da ƙoƙarin maida murtani. Rikicewa Smart ya sake yi illahirin jikinsa ya shiga rawa, sai ya nema canja salo akan fiye da abinda yake yin. Anan ne fa Lulu ta dawo hayyacinta, jikinta daya fara rawa ta fisge taja baya, sai kuma ta shiga kallon gadon da sauri, cikin ƙarfin hali da dafe kai shima Smart ya tashi zaunen. Masifa take son masa, amma bata da wani ƙarfin yinta, sai kawai ta sakar masa kuka.
(Ya ALLAH) ya ambata a zuciyarsa da janye hannunsa da ya dafe goshi ya ɗago idanunsa da sukai matuƙar kaɗawa ya zuba a kanta. Lips ɗinsa na ɗan rawa ya ce, “Mawaddat…” yama kasa ƙarasa abinda yake son faɗar, sai kawai ya sake dafe kan tare da komawa ya kwanta..
Hakan da yay sai ya sa wani irin takaici sake mamaye zuciyar Lulu wato ma kenan yayi hakanne dama da shiri. Tattaro dukkan ɓacin ranta take a maƙoshi, amma ta kasa furtawa, sai kawai ta tura kanta cikin ƙafafunta ta sake sakin kuka. Har cikin tsakkiyar ransa yake jin kukan nata, ga bala’in daya ƙulle masa ciki ya sashi kasa koda iya motsawa, jin ta sauka a gadon ya sashi buɗe idanun nasa da ƙyar, dai-dai nan ta buɗe ƙofar ɗakin ta fita tare ba banging nata da ƙarfi har sai da ya rumtse idanunsa. Har aka kira asuba ya kasa tashi saboda halin da yake ciki, ita kuma bata dawo ba, addu’a kawai yake ALLAH yasa ba ɗakin yaran ta tafi ba, duk da baya jin zatai hakan. Duk da halin da yake ciki shi ya cancanci tausayi amma shi ita yake tausayawan, dan yau ya sake tabbatar da akwai wani abu a ranta da yasa take ma tsanar maza da ƙara ƙaimi wajen son ɗaukar mataki akan masu fyaɗe. Hakan kuma nada alaƙa da cin kashin da takema ƴan aikin gidansu, dan tun a wancan karon dama ya lura tafi taka mazan fiye da matan. Da ƙyar yay dauriyar sakkowa ya nufi bathroom ɗin ɗakin, ko kayan bai cire ba ya sakar ma kansa ruwan sanyi, ajiyar zuciya ya dinga saukewa a jajjere, yafi mintina goma kafin ya kashe shower ɗin ya zame kayan jikinsa, dole ya tsaftace jikinsa sannan ya fito, har yanzu dai da alama cikin nasa bai saki ba, a haka yay dauriyar fita a ɗakin ɗaure da towel ɗinta. Falo ya fara dubawa ko tana nan, amma bai ganta ba, sai kawai ya yarda wajen yaran taje. Lips ɗinsa kawai ya cije ya koma bedroom ɗinsa, sai kuma a mamakinsa ya ganta kwance anan. Dan yana buɗe ƙofar tana miƙewa zumbur cikin ɗan barcin da ya figeta bayan ta gama shan kukanta a dalilin abubuwa da yawa na rayuwarta da suka shiga dawo mata wanda bazata taɓa mantawa da su ba.
“Nan ma biyo ni kayi? Aliyu ni zaka shiryama tuggu kamin fyaɗe! Wlhy ka sani nafi ƙarfinka kai da ma duk ire-iren ka, kuma da ga yau idan ka sake tunanin raɓata sai na ɗauki mataki a kanka dan zan iya maka illa, dan haka ka kama kanka kwanakin nan su cika batare da ka rasa wani sashe na jikinka ba!”.
Sororo Smart yay kawai yana kallonta, yanda take maganar da dukkan gaskiyarta ga hawaye tanayi kuma, kalmar “Zan iya illataka Aliyu! Wlhy zan iya illata ka kamar yanda na kashe wancan tsinannen” ta sashi dawo hayyacinsa. Sai kuma ƙirjinsa ya shiga bugawa, amma sai yay jarumtar dannewa wajen faɗin, “Mawaddat relax ni fa mijinki ne, ki sani ni ba irin waɗancan da kike tunani bane, ALLAH ya halatta min ke duk abinda zan miki bada nufin cutarwa bane. Mawaddat aure yanada tarin abubuwa da suka banbanta da abinda zuciyarki ke iya hasaso miki. Dan ALLAH ki bar kukan nan haka ki nutsu bayan munyi salla muyi magana”.
“Bazanyi magana da kai ba Aliyu, bakuma zan sake ganin mutuncinka ba wlhy, ban san haka kake ba ai kaina da ban ɗauke ka a yanda na fara ba….” fuuu ta fice a ɗakin nan ma tai banging ƙofar da ƙarfi har sai da ya ɗan zabura. Ya jima shiru abubuwa da yawa na masa kai da kawo a zuciya har aka fara ƙoƙarin shiga salla. A gaggauce ya shirya sai dai bazai iya fita massalaci ba dan cikinsa yay masifar ƙullewa dole a gidan yay salla. Bayan ya idar yana son zuwa inda take amma yana gudun kar yaran can su fahimci mike faruwa. Dole ya haƙuri akan har sai sun wuce, dan haka ya hau gado ya kwanta. Abu kamar wasa sai ga ƙaramar magana ta zama babba, dan kuwa dai zazzaɓi ne mai zafin gaske ya lulluɓe Smart harda su rawar sanyi………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣5️⃣
………Lulu duk da ranta a dagule yake tayi dauriyar dannewa saboda yaran, kasancewar Maryam akwai hankali tunda daddare ta tsara musu su tafi yau suba ma’auratan waje, sai kuma akai sa’a har su Amrah suka fahimceta. Koda gari ya waye sukaga basu fito ba basu damu ba suka gyara gidan tsaf sukai break fast. Nasu sukaci suka shirya musu nasu a table. Sun kammala kenan Lulu ta fito. Gaisheta sukai su duka cikin haɗa baki, ta amsa musu tana murmushin ƙarfin hali, dan girmamawa na ɗaya da ga cikin abinda Lulu keso gana ƙasa da ita. Wannan kuma shine mataki na farko da dangin Smart suka kama mata zuciya da shi, yau gashi har ƙannenta sun kwatanta abinda bata taɓa gani ba. Kamar yanda suka tsara Maryam ce ta sanar mata zasuje gidan ƙunshi su taho da mai ƙunshi da tace tana so. Lulu bata kawo komai a ranta ba ta ce, “Da sassafen nan kuma Maryam. Ku bari sai anjima ni ƙunshin ma kamar na fasa kuma”.
“Kai aunty dan ALLAH karki fasa. Ai zamuje ne dan ta sani inma tanada wani aiki kinga ta kammala da wuri bawai yanzu zata zo ba”.
“To shike nan, amma har ku duka zakije?”.
A tare suka amsa mata da eh. Key ɗin motar ta dake a falon ta miƙama Amrah dan sun iya driving duk da dai ba basu mota ake ba sai ta kama. Cikin gargaɗi tare, “Banda ganganci Please”. Dariya kawai su Afrah sukai dan sun san dai aunty Lu.. ɗin su indai tuƙin ganganci ne ita ɗin master ce. Sallama sukai mata suka fice, dama sun fidda kayansu tun ɗazun..
Kwanciya tai a falon batare da neman abincin da zata ci ba duk da kusan goma ne yanzun. Tana a wajen kwance ba barci take ba har sha biyu, tunanin abubuwa kawai take daban-daban, babu alamar su Maryam dan haka ta ɗaga waya tai kiran su Amrah. Cikin dariya suke sanar mata ai su suna ma gida, sai da suka fara ajiye su Asma’u ma sannan. Shiru kawai tai da mamakin wai ita yaran nan zasu yaudara, sai kawai tai ƙwafa ta yanke kiran. Ɗan jimm tai saboda abinda take jiyowa kamar ƙaƙarin amai, kamar zata share sai kuma ta miƙe da sauri jin abin na ƙaruwa. Sam batai tunanin Smart na gidan ba, ɗakin nasa ta shiga dan anan take jiyowa, nan ɗinne kuwa a cikin toilet, mamaki ya kamata duk da matsanancin haushinsa da take ji na abinda ya faru sai ta nufi bayin. Sosai gabanta ya faɗi, har bata ma san sanda ta afka bayin ba inda yake.
“Lafiya kake kuwa?”.
Bai iya bata amsa ba dan ya gama galabaita da aman, dole ta ajiye komai da ke ranta kuma ta shiga taimaka masa ya wanke bakinsa da fuska, da taimakonta ya fito ya sake hawa gadon ya kwanta.
“Please lulluɓe ni”.
Ya faɗa da ƙyar. Lulluɓe san tai hankalinta a tashe, dai-dai nan kiran Ahmad ya shigo wayarsa, har ya lumshe idanunsa ya buɗe, ita ya kalla yayinda ita kuma take kallon wayar. “Waye?”. Ya faɗa a hankali. Wayar ta miƙo masa da faɗin, “Besty kasa”. Sake maida idanun nasa yay ya lumshe da faɗin, “Ahmad ne ɗaga”. Kafin ta ɗaga ɗin wayar ta yanke, tana ƙoƙarin kira Ahmad ɗin ya sake kira. Ɗagawa tai ta saka a Hansfree da faɗin “Hello”. Daga can Ahmad ya amsa mata duk da yayi mamakin jin wayar a hannunta. Gaisheshi tai da sanar masa bai da lafiya.
Hankali tashe Ahmad ya ce, “Ya ALLAH gani a ƙofar gate ai”.
“Okay to bara ina zuwa”.
Tai maganar tana yanke kiran. Wayar ta ajiye ta miƙe, Smart da ke saurarensu ya buɗe idanunsa a kanta, a hankali ya furta “Please kar ki fita a haka kisa hijjab”. Harararsa tai batare da tace komai ba ta fice. Samun kanta tai da shiga ɗakinta ta ɗauka hijjab ɗin ta saka sannan taje ta buɗema Ahmad ɗin. Ita tai masa rakkiya har ɗakin Smart ɗin ta fito ta barsu.
Bayan Ahmad yay masa sannu ya ce, “Tashi zakai mu tafi asibiti”.
Kai Smart ya girgiza masa yana ɗan buɗe idanunsa, “Basai naje asibiti ba zai bari da kansa in sha ALLAH. Tunda ma na samu nayi aman shike nan”.
Ahmad ya riga da yasan miye matsalar Smart ɗin. Dan haka yay shiru kawai. Dai-dai nan Lulu ta shigo ɗakin da sallama. Amsa mata Ahmad yayi. Ta ajiye tray data haɗo abincin tana faɗin “Ya sanar maka abinda ke damun nasa kai ko?”. Murmushi Ahmad yay da bata amsa. “Kin san mutumin naki ai, yanzu ma fama nake da shi muje asibiti yaƙi”.
Kallonta takai kan Smart, ganin shima ita yake kallo ƙasa-ƙasa saita janye nata da ɗan taɓe baki. Shi Ahmad ma sai suka bashi dariya. Dan haka ya miƙe. “Inaga bashi abincin ni bari naje na samo masa magani, dan tunda yace bazaije asibitin ba to bazai je ba”. Bai jira cewarta ba ya fice. Ɗan hararar Smart Lulu tayi, a taƙaice ta ce, “Ka tashi”. Sake buɗe idanun nasa yay ya zuba mata su na kusan minti ɗaya, ita kuma ta kauda nata dan tun ɗazun yanda idanun nasa launinsu ya sake canjawa suka fito a sak na macizan da take kiransu taji bata son ya kalleta. Hannu ya miƙa mata alamar ta kamashi. Kamar zata share sai kuma dai ta kama dan ya ɗan bata tausayi kuma. Harya faɗa kamar wanda ya kwana biyu yana ciwon. Shayin data haɗo masa ta miƙa masa, babu musu ya amsa tare da motsa lips ɗinsa kaɗan ya ce, “Thanks”. Koda ta miƙa masa soyayyan doyan sai ya girgiza mata kai alamar bazai ci ba. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta maida doyar ta ajiye. Tana zaune ta ɗan juya masa baya tana latsa wayarta har ya kammala, kofin ya miƙa mata ya koma ya kwanta, ta tattare kayan ta fita da su, a lokacin kuma Ahmad ya dawo, ruwan da ya buƙata da Smart ɗin zai sha magani ta ɗakko masa, da ga haka ta koma falo tai zamanta…
Ahmad bai bar gidan ba sai da Smart ya samu barci, bayan wucewarsa Lulu ta leƙasa, ganin yay barci ta ɗan sauke ajiyar zuciya da hararsa kamar yasan tanayi. Ɗakinta ta nufa ta ɗan kwanta itama dan shirun gidan kuma duk sai yay mata babu daɗi. Kusan a tare suka tashi bayan la’asar, tai wanka tai salla dan yanzu kam Alhamdullah, idan ma tai kamar zatai sakaci lokaci ya wuce sai taji duk babu daɗi har sai ta tashi tayi sallar take samun nutsuwa. Cikin skert dogo baƙi da ƙaramar top baƙa itama datai mata ɗas a jiki ta fito, kanta babu ɗankwali sai gashin da ya sha gyara yanata walƙiya. Wayar da take dannawa tana charting da aunty Naja’atu yasa bata lura da shi ba har sai da takai zaune. Shiko tun fitowarta ya zuba mata idanu, murmushin da take yi ya matuƙar ƙawata ƙyawunta da motsa rauninsa. Hakama kwalliyar tata ta ɗauki hankalinsa duk da ita hakan normal ne a gareta badan wani birge miji ko wani abu ta saka ba tunda dai sune kayanta na koyaushe fiye da atamfa. Ƙaramin gyaran murya da yay ya sata farga da shi, dariyar da takeyi a hankali ta haɗiye ta ɗago idanunta da sukai wani tar-tar da su da haske mai ɗaukar hankali kasancewar duk yau da ba’asha komai ba.
“Dama haka ake jiyyar mara lafiya Madam?”.
Hararsa ta ɗanyi da taɓe baki. “Ka dai san mai jiyyarka ba dai Mawaddat ba”.
“Uhm hakane ashe Ahmad ne kuma fa”.
Ya faɗa yana danne dariyarsa.
Sake taɓe bakin tai taƙi cewa komai. Da ga haka shiru ya ratsa falon, yana tunanin faɗa mata zancen tafiyarsa da ya taso ne, dan abinda ma ya kawo Ahmad kenan, amma sai yaga bari dai ya bari ta sake nutsuwa ko zuwa gobe in sha ALLAHU. Kusan mintuna goma ya sake takalota da faɗin, “Ba abinci gidan ne? Ina kuma yaran nan banji motsinsu ba?”.
Yanzu kam kai tsaye ta bashi amsa da “Sun wuce”.
“Abincin fa?”.
“Na daina girki a gidan nan”.
“Miyasa?”.
“Ba sai da dalili ba, dama can ra’ayi nayi, yanzu kuma na daina sai ka bari sai ka auro matar da zata maka”.
“Kishiya kike sha’awa kenan?”.
Kamar bazata tanka masa ba sai kuma tai murmushi. “Sai dai idan yau zaka aurota ko gobe kafin cikar jibi da zan ƙara gaba maybe wasu su kalleta a matsayin hakan”.
Murmushi kawai ya saki, maimakon cewa wani abu akan batun nata sai cewa yay “Bani furar da Ahmad ya kawo Please dan yunwa nake ji”. Kamar bazata je ɗin ba sai kuma ta miƙe. Babu jimawa ta dawo da furan da kofi ta ajiye masa ta koma inda ta tashi. Television ta kunna shi kuma ya zuba furar ya fara sha.
“K mi kika ci?”.
“Ba buƙata”.
Ta faɗa a takaice.
“Okay amma da kinsha furan da ga gidan Ammah ya amso ta”.
Ɗagowa tai ta kallesa. Sai ya jinjina mata kai alamar tabbatarwa.
“Gama ka bani kofin bana jin sake tashi”. Ta faɗa tana maida kanta ga wayarta. Bai sake magana ba har ya gama ɗin ya zuba mata, sai dai bata da yawa dan haka ya miƙe da kansa yaje kitchen ya sake ɗakko wata ya ƙarasa cika kofin ya miƙa mata. Hankalinta nakan waya take shan furar harta shanye, sake ƙarawa tai. Sai da ta shanye ta biyun yay ƙaramar dariya da faɗin, “Babu wata furar Ammah da kika sha yarinya a titi ya sayota”. Da sauri ta kallesa tana yamutsa fuska, ya sake sakin dariya da nuna mata 8-10. Filo ta ɗauka ta jefa masa da yin ƙwafa tana harararsa, sai kuma ta fara ƙaƙarin amai shiko ya cigaba da dariyarsa. Kofin takai kitchen ta wanke dan bata ƙaunar ƙazanta, duk da kuwa aikin na cimata rai dan ma yana ƙoƙarin taya ta ne, tun tana ƙorafin mai aiki har ma ta bari tunda dai taga kwanakin sun ƙare mata a gidan. Falon ta dawo ta cigaba da ɗan kallon abubuwa a TikTok. Shiko yana kwance shiru ya zuba mata ido ta ƙasa kawai yana kallonta. Kiran sallar magrib ne ya tadasu su duka. Smart ya wuce massalaci ita kuma ta tafi ɗaki. Bai jimaba ya dawo gidan saboda abinda ke damunsa ba wai ya gama sakinsa bane gaba ɗaya, jarumtar da ya saba ce kawai ta dannewa. Bai samu Lulu a ɗakin ba dan itama tana nata ɗakin a cikin makamancin irin nasa yanayin koma ace wanda yafi nasan. Dan wani abu ne ke faman ratsa mata jiki mai ban mamaki. Ga tsigar jikinta sai faman tashi take kamar mai jin sanyi. Al’amarin kamar wasa sai ya fara neman fin ƙarfin Lulu, dan da ƙyar ta iya tashi tai sallar isha’i……..✍️
😵💫Lulun mu muya hwaru kuma🥲?
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣6️⃣
……..Tana idar da salla falo ta koma a daddafe, a ganinta ko zata samu sassaucin abinda takeji ɗin, sai dai kamar ma ana ƙara iza mata wutar masifa ne a cikin jininta. Saman 3sitter ta haye tare da dunƙule jikinta waje ɗaya tana jin hawaye na ciki mata ido. Ta rasa wannan wace irin masifa ce haka mara daɗin kwatance.
Ana idar da salla shima Smart gidan ya nufo, dan har yanzu ba wani ƙarfin jikinsa yake ji ba, tunda ya shigo falon idanunsa suka sauka a kanta, ya ɗan yi jimm yana kallonta kafin ya ƙaraso ciki sosai yana ambatar sunanta. Bata motsa ba, hakan ya sashi fahimtar babu lafiya. Har inda take ya ƙarasa, ya kai zaune a kujerar da take yana mai leƙa fuskarta. Hankalinsa ne ya tashi ganin tana hawaye.
“Ya Salam kuka kuma? Baki da lafiya ne?”. Yay maganar yana riƙo hannunta data dafe cikinta, gaba ɗayanta ya ɗago zuwa jikinsa, sake shige masa tai cikin yanayin kamar mai rawar sanyi. Hakan sai ya bashi mamaki dan ba halinta bane hakan sam kusanta kanta da shi, sannan bai manta da gargaɗinta na ɗazun akan karya sake taɓata ba. Jin yanda tama kanannaɗe masa a jiki tana shashshekar kukan da ke ratsa masa zuciya ya sashi kasa iya cewa komai. Kusan mintina uku suna a haka kafin ya ɗago fuskarta dake kwance saman ƙirjinsa hawayenta na sauka masa, itama ɗagowa tai a hankali suka zubama juna ido cikin wani yanayi mai wahalar fassara. Hannunsa ya ɗaura saman fuskarta cikin ɗan lumshe idanu da buɗewa ya furta, “Mawaddatan’warahmah!”.
“Uhhmyim”.
Ta amsa shi acan ƙasan maƙoshi tana lumshe idanunta hawayen da suka sake cikashi suka zubo. Jiyay gaba ɗaya hankalinsa ya sake tashi, cike da damuwa ya ce, “Har yanzu kina fushi da ni akan abinda ya faru shiyyasa kike kuka ko?”.
Idanunta da sukai mugun canja launi ta sake buɗewa sosai a kansa, fuskarta a ɗan taɓe kamar mai son sakin kukan shagwaɓa ta girgiza masa kai.
“To mike damunki? Ko baki da lafiya?”.
Maimakon bashi amsa sai ta kamo hanunsa ta ɗaura a saman cikinta. Kallon cikin yay da sauri, sai kuma ya dubeta da faɗin, “Yana miki ciwo ne”. Kamar ba Lulun nan da ya sani masifaffiya ba, ta ƙara manna hannunsa akan cikin nata muryarta data koma can ƙasan maƙoshi na ƴar rawa-rawa ta ce, “Hydar yan….” sai kuma ta kasa ƙarasawa kawai ta sakar masa kuka. A karo na farko gabansa ya faɗi, ya kamata zai tayar yana faɗin, “Kinga tashi muje asibiti”. Girgiza masa kai tayi da sake nannaɗewa a jikinsa tare da kai hannunta saman gashin da ke kwance a fuskarsa luf-luf ta zubawa lips ɗinsa idanunta da sukai matuƙar juyewa fiye da yanda idan tasha kayayyakin ta sukeyi. Sororo yake kallonta, dan wannan kam shi shaida ne ba ɗabi’a ce ta ta ba. Yanda ta motsa ƴan yatsunta cikin gashin sajensa ya saka tashi tsigar jikin yamutsawa, tare da harbawar zuciya, abinda ke ƙoƙarin lafawa da ya girgiza ƴan maza a yinin na yau na ƙoƙarin zaburowa. (Anya ba wani abu daya fi ƙarfin kan yarinyar nan ta sha ba?) wani sashe na zuciyarsa ya ayyana masa, sai kuma yaji hakan bai kama hankali ba… (To mike faruwa?) Ya sake ayyanawa, sake ji yay zuciyarsa ta motsa, dan kuwa kalaman Ahmad na daren jiya ne suka shiga maimaita kansu a kwakwalwar sa, sai kuma furar da suka sha, tabbas akwai alamar tambaya… Saukar lips dinta saman nasa a bazata ya katse tunaninsa, sai riƙon da tai masa mai lafiya daya sakashi yin baya gaba ɗayansa ya zube a kujerar…..
Dama mai neman kuka ne aka jefa da kashin awaki, kuma kamar Lulu ta kawo kuka ne gidan mutuwa. Sai ya kasance ita da aka saka a tarko ma ya fita rikicewa. Ganinfa ƙurar yaƙi na neman fara tashi a muhalin da bai kamata ba bai ma san lokacin da ya bar falon da ita ba zuwa bedroom ɗinta ba…..
Sai da ya gama tabbatar da ta shiga hannu fiye da yanda yake buƙata, duk da harga ALLAH bada saninsa ta sha abinda ya kaita ga miƙa wuyar ba cikin sauƙi. Gashinta da ke cikin ribbon ya wargaza tare da duƙo fuskarsa gab da tata suna kallon juna, murya can ƙasa kamar zai saki kuka ya furta, “Kin yarda Aliyu Hydar ya zama Mawaddat? Mawaddat ta zama Aliyu?”.
Shiru kamar bazatace komai ba, sai kuma ta ɗan buɗe idanunta data lumshe a kansa itama, so take tai nazari akan maganar tasa amma ta gagara samun kowace irin dama daga gangar jikinta zuwa ƙwaƙwalwa, sai ma hannunta ta ɗaura akan nasa tana girgiza masa kanta. Itama acan ƙasan maƙoshi ta ce, “Ina jin shakku”.
“Kar kiji shakkar komai, Aliyu na *_SONKI_*, yana kuma buƙatar ki matsayin uwar ƴaƴansa abokiyar rayuwa ta har abadan Mawaddatan’warahmah. Na miki alƙawarin bazaki taɓa dana sanin zama mallakin Aliyu ba, in sha ALLAH sai na nunama duniya Mawaddatan’warahmah ba Lulu da suke kallo kawai bace akwai wani babbar nagarta tattare da ita”.
Murmushi ta saki mai ɗan sauti ta buɗe idanunta data sake rufewa suka zubama juna ido. “Mi kake nufi Aliyu?”.
“Baki LABARI kawai zai baki, amma gangar jiki tabbatar wa zatai kafin zuciya ta amayar da sirrin da ke cikinta. Alƙalamin ƙaddara ya jima da bushewa Mawaddat, hakama takardu sun daɗe da ɗaguwa. Miya rage garemu? ƙarasa zuwa filin yaƙin da zai bayyana Aliyu mijin Mawaddat ne kawai domin hutar da zukata masu farautar igiyar da UBANGIJI ya riga ya gama ƙadarta ƙulluwarta tun kafin haihuwar mu…..”
“Bana gane zance a curkuɗe ka buɗemin kawai Aliyu, kana saka ni a duhu da dogon nazari a duk sanda ka ɗauki wannan tsagin na curarrun kalamai”.
Goshinsa ya kai saman nata, hancinsa na gogar nata suna shaƙar numfashin juna. Ya saki murmushi mai sauti. “Ki bani damar baki gaba ɗayan kundin curarrun kalamai na, ni kuma zan kasance miki malami mai fassara miki su feji bayan feji a mabanbanta zangunan da masu neman ilimin kan jima basu cimmawa ba Please Mawaddatan’warahmah, na fara gazawa, ni kuma bana buƙatar shiga makarantar da babu shaidar samun damar ɗaukar darasi a cikinta, dan zata kasance min tamkar ɗan yawon buɗe ido ne kawai”.
“Mi kake buƙata da ga gareni?”.
“Yarda”.
“Karka zama bahagon malami”.
“Ki zama ɗaliba mai kaifin basirar ƙarɓa da haddacewa, domin ranar amsar sakamakon jarabawa ki ɗauki first class”.
“Jarumta da kaifin basira a jinina suke”.
“Ni mai yarjewa ne ga dukkanin furucinki, domin tabbatar miki da hakan muje matakin farko na tabbatarwa *_ALJANNAR DUNIYA TA_*”.
Saukar lips ɗinsa akan nata ya hanata damar furta abinda ta so faɗar, hannu biyu ta amshesa kasancewar ita a karan kanta bata sana wacece ita a wannan fagen yaƙin ba. Abinda kawai ta sani gangar jiki da zuciya duka sun karɓa saboda hakan ne mafi ƙololiwar miradinsu a wannan gaɓar bisa tirsasawar abinda tasha batare da sani ba. Al’amari fa kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba, dan su duk biyun cikin mata kai kowa ya fara kaima ɗan uwansa hari irin na ƙasa da ƙasa. Kafin kace mi sun birkice ma juna daga haka fa labarin ya canja a yanda su duka ba haka sukai tunanin rubutuwarsa ba, dan kuwa dai tabbas wannan daren yazo ne a bisa rubutun alƙalamin ƙaddarar da basu isa canjata ba koda ace sun so hakan. Lokacin da al’amari yay nisan zango Lulu ta fara dawowa a hayyacinta da fahimtar mike shirin faruwa. Sai dai me, Smart ya kai matakin da _Uranium_ ya ke shirin jefawa fa a ƙasarta ba nuclear bomb kawai ba.
“Aliyu! Aliyu!! Hydar!!” ta shiga ƙwala kiran sunansa a matuƙar firgici na fita a hayyaci numfashinta na barazanar barin ƙirjinta saboda tsabar shiga firgici, sai dai ina wannan yaƙin na bashin gaba ne ba na kece raini kawai ba. Kuka ta fashe da shi da cigaba da kwala kiran sunansa da magiya kai harma da tabbatar da zata halakashi amma ina, turnuƙun ƙurar yaƙi ta lulluɓe ji da ganin idanu da kunnuwa sa, yafayi alƙawarin yau sai ya kai duk wani shegen tsageran kafiri ƙasa ko shima a lissafashi a jerin manyan jaruman mayaƙa da suka amshi turar ƙasa data MUSULUNCI a hannun dama. Wannan da shi ake kira TURNUƘU faɗan ibilisai, yaro bai gani ba balle ya raba🚴….
A wannan turnuƙu duk wani wanda Lulu kema kallon defender a rayuwarta harma da ƴan koron abi yarima a sha kiɗa irinsu Deen sun sha kiran kawo ceto sai dai da alama ko fankar ɗakin tsoron ya hanata iya juya kanta balle su da ke nesa da jinta maybe ma wasu suna can a cikinsu suna mafarkin aljanna da naman kaji da madara😁.
(ALLAH kasa munada rabon zuwa ba’a mafarki kawai ba mu da masoyan mu baki ɗaya💫. Amma fa safiyar gobe dole a sake maimaita ƙaramin yaƙin basasa kona wucin gadi ne tsakaninmu da Smart team sai sun mana dalla-dallar yanda akai aka kawo mana wannan yaƙin sunƙurun haka🚴🚴)
____________★
Zaune take hakimce uwa wata sarauniya a makeken falonta tana ma ƴaƴan itatuwa tsinci ɗai-ɗai. Mai aikinta na daga ƙasa tana tausa mata ƙafafu. Kamar wanda aka jeho da ga sama ya faɗo falon, zaburar da mai aikin tata ta ɗanyi ne ya saka Dada janye idanunta da ga kan tv ta dubeta, masifar tata tai shirin balbaleta da ita, sai kuma tai tsit saboda gyaran muryar da yayi. Gaba ɗayanta ta juyo ta dubesa, sai kuma ta saki baki alamar mamaki.
“Sulaiman? Kai ne?”.
Murmushi yayi a karo na farko, sai kuma ya cigaba da takowa cikin falon. Kafin ma wani a cikinsu yay magana mai aikin Dada ta miƙe zumbur dai-dai yana kaiwa zaune a kujerar kusa da Dadan da faɗin. “Ni ne fa Dada. Mun sameku lafiya?”.
“Sulaiman bakai fushi ba kenan?”.
Ƙaramar dariya yayi da kamo hanunta cikin nasa, cike da sauke murya ya ce………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣7️⃣
………“Dada wane ɗa ne zai yi fushi da iyayensa. Balle ma ke nasan baki da laifi akan wannan al’amarin sam.”
“Naji daɗi da ka fahimci haka Sulaiman, dan babu ta yanda zan goya bayan bare sama da jikana. A yanzu haka koda akai min katanga da bibiyar halin da kuke ciki ban zauna ba, kuma nayi alƙawarin sai Mawaddat ta dawo hanun Tajuddeen matsayin mata dan bazan taɓa amsar waninsa ba”.
Wani irin farin ciki ne ya ratsa Alh. Sulaiman, dama shi yasan Dadarsa na tare da su. Dada dake murmushin itama ta ƙara ƙasa da murya da faɗin, “Labari ma mai da ɗi……” Tsaf ta kwashe yanda sukai da Lulu ta sanar masa. Baima san sanda ya lailayo wata ashariya ya dire ba a gaban mahaifiyar tasa. Ya ce, “No wander naga yaron nan Yousuf nata rawan kai, ashe shegen shine ya ƙulla komai”.
“Wlhy kuwa, nima abin ya girgizani Sulaiman. Amma ka kwantar min da hankalinka jibi da kaina zanje na ɗakko Mawaddat ko yaron nan na yawo da ubansa a baya sai ya saketa”.
“ALLAH ya barmin ke Dada ta”.
Ya faɗa cikin wani irin matsanancin farin ciki. Gaba ɗaya damuwarsa ta shafe ma. Bai iya dogon Zama ba a gidan bayan sun ɗan tattauna akan abinda ya samu Baba da ta bashi labari ya wuce gida kasancewar dare ya fara yi, yana tabbatar mata gobe idan ALLAH ya kaimu Tajuddeen zai zo ya gaidata, da dai ya ɗauki fushi bazai sake zuwa wajensu ba, amma yanzu zai lallasoshi, dan zai sanar masa ƙoƙarin da take masa. Sosai Dada taji daɗin hakan, dan ita kam ALLAH ya jarabceta da shegen ƙulafucin ƴaƴanta da ma jikokin duka. Sai dai kuma matan ƴaƴan nata da babu wanda ta ɗagema hula a rashin mutunci, juyasu take san ranta kamar waina a tanda kamar yanda ta kame ƴaƴan nata ram a hannu sai yanda tace musu, Alh. Sulaiman ɗin nema dai kan botsare mata a wasu lokutan dan shima dai halayyar tata ce ya ɗebo tsaf. Shiyyasa takanji shakkarsa duk da kasancewar itace ta haifesa, san nan tana sonshi sosai wannan a bayyane yake a wajen kowa ma, dan sam idan rashin mutuncinsa ya tashi ba raga mata yake ba tun ma yana ƙaraminsa, balle yanzu da yake jin ya gawurta da tumbatsa a gidan ta fanin dukiya da yin suna a cikin ƴaƴan nasu. Amma a kullum Dada bata ganin laifinsa sai ma bashi goyon baya da takeyi….
__________★
Matuƙar tashin hankali Smart ya shiga a lokacin da ya fahimci halin da Lulu ke ciki. Ta sanƙame masa babu alamar rai tattare da gangar jikinta, da ƙyar tunanin zuba mata ruwa yazo masa a rai, sai dai koda ya shafa mata ruwan ma shiru kake ji. Gaba ɗaya ruwan ya zazzage mata zuciyarsa na wani irin dokawa tamkar zata faso ƙirjinsa ta fito waje. Wata irin zaburowa tai jikinta na jijjiga. A tsahon rayuwarsa baya jin ya taɓa fuskantar makamancin farin ciki da tashin hankali masu gogayya da juna irin haka. Duk yanda yake tunanin iya shawo kan matsalar hakan ya gagara, dan yanayin nata ya wuce dukkan tunani. Yasan idan yace zai ɗauketa zuwa asibiti a wannan halin bazai ma iya driving ba, to yama manta motar su Amrah sun tafi da ita gida, dan haka ya shiga neman wayarsa. Da ƙyar ya iya samota a ƙasa harta fashe. Bai damu ba ya shiga neman Ahmad dan shine kawai yazo masa a rai.
Shigowar kiran ta saka Ahmad kwashewa da dariya, amma daya ɗaga sai ya dake dan shi duk tunaninsa Smart ya gano ne. Sai dai kuma jin muryarsa ta saka gabansa faɗuwa. Da sauri ya ce, “Mawashi Are you okay?”.
“I am not Ahmad. Ina cikin tashin hankali ka taimakeni kazo mukai Mawaddat asibiti, Ahmad akwai matsala wlhy na saka yarinyar mutane a masifa….”
Sosai zuciyar Ahmad ta jijjiga, amma sai yay saurin tarar numfashin Smart da faɗin, “Kaga Aliyu dan ALLAH ka kwantar da hankalinka, ka faɗamin mike faruwa ne. Ka sakani a tashin hankali nima….”
Cikin ƙaraji Smart ya katsesa da “Mi kake son sani ne Ahmad!! Ina faɗa maka kazo muje asibiti kana gaya min na kwantar da hankalina na sanar maka mike faruwa?. Ahmad ka taimakeni karna rasata, bazan iya yafema kaina ba idan hakan ta kasance”. Ya ƙare maganar cikin sanyin murya hawaye masu zafi na gangaro masa a karo na farko…
Kaɗan ya rage Ahmad yin aman zuciyarsa. Muryarsa na rawa da daburcewa ya ce, “Ka.. ka yi haƙuri gani nan zuwa.” baima jira amsar Smart ɗin ba ya miƙe tare da figar jallabiya ya saka. Karo suka kusan ci da Coach da ke ƙoƙarin shigowa ɗakin nasa, da mamaki ya ce, “Ahmad kana lafiya kuwa? Ina zaka haka?”.
“Yaya babu lafiya, na aikata babban kuskure wlhy.”
“Kai miye haka wai, nutsu mana”.
Coach ya sake faɗa yana riƙo Ahmad da ke ƙoƙarin turesa ya fita.
“Yaya dan ALLAH kayi haƙuri idan na dawo zan maka bayani. Aliyu ne ya kirani…”
“Kai bana son shashancin ka nutsu kamun bayani mana”.
Rasa mi Ahmad zaice yayi, sai kawai cikin matuƙar gundura ya ce, “Asibiti yaya. Asibiti zan kaisu, na tabbata koma minene yanada alaƙa da abinda na aikata wlhy. Dan girman ALLAH ka barni naje”.
Hankalin Coach ya fara tashi shima, dan Ahmad yana magana ne kamar zai yi kuka.
“Innalillahi wa-inna ilaihiraji’un. Ahmad Please ka faɗa min mike faruwa? Miya samu Aliyun ne? Mika aikata masa kuma?”.
“Yaya nayi kuskure, abu na saka musu a fura, bana raba ɗayan biyu koma miya tada hankalin Mawashi nada alaƙa da abinda na aikata ɗin. Yaya kamarfa kuka yakeyi da tabbatar min zai rasata. Yaya ka barni naje dan ALLAH”.
Kai Coach ya dafe domin ya samu amsar abinda ya kawoshi sashen ƙanin nasa dama. Dan dama matarsa ce ta bashi maganin da Ahmad ɗin ya yarda ɗazun batare da ya sani ba kuma an ɓalla maganin, kasancewarta likita yasa hankalinta tashi fahimtar maganin datai kona minene. Taso danne zuciyarta ta binciki Ahmad ɗin ita kaɗai amma saita kasa haƙuri ta tunkari mijin nata da batun shine dalilin fitiwarsa zuwa inda Ahmad yake. Yanzu kuwa jin zantukan Ahmad ɗin ya tabbatar masa su Aliyu ya bama maganin ke nan. Ba lokaci bane na dogon tunani, dan haka ya ciro wayarsa da ga aljihu yana faɗin, “Kaga bari Khadijah tazo kuje tare, yanzu dare yayi duk asibitin da zakuje zaku iya fuskantar matsalar ganin doctor.”
Tuni Lulu ta sake fita a hayyacinta wa Smart, zuwa yanzu kam koda ya zuba mata ruwan ma batako motsa ba. Sai kawai ya dafe kansa dake wata irin masifar sara masa. Ya auna kiran Ammah sau shuri masaƙi zuciyarsa na gargaɗinsa. Hakama Abba. A wannan halin ya tsinkayi horn ɗin da yake ƙyautata zaton na Ahmad ne. Zumbur ya miƙe ya fito, dan yasan dole sai ya buɗe masa gate ya shigo. Doguwar riga ya samo ya saka mata, dama shi tuni ya suturta nasa jikin. Yana buɗe gate ɗin bai jira ƙarasa shigowar Ahmad ɗin ba ya juya cikin gidan da sassarfa. Fitowa aunty Khadijah tai tabi bayansa, yana ƙoƙarin shigewa bedroom ta kirayi sunansa. Da sauri ya juyo dan shi idonsa ma yay rufewar da bai kula da ita ba, sannan ya manta ma ita likita ce har sai da tai masa bayani. A tare suka shiga ɗakin, ta ajiye ɗan akwatin dake hannunta ta haura gadon ta ɗagota Lulu zuwa jikinta….
Smart da gaba ɗaya dauriyarsa ta gama ƙarewa cikin sarƙewar murya ya ce, “Aunty mun rasata ko?”.
“A’a Aliyu da ranta. Dan zuciyarta na harbawa suma tai kawai. Amma miya firgitata haka? Dan irin wannan sumar mai nauyi mummunar firgici ko tsorata mai tsanani akan abinda mutum baya so ke kawota”.
Kasa bata amsa yay dan tana cikin mutanen da a rayuwa yake matuƙar ganin girma da jin kunya. Itama fahimtar hakan ya sata cewa, “Shike nan ɗan bani waje mugani”. Babu musu ya fita, inda ya samu Ahmad a falo na faman kai kawo. Da sauri ya taresa da tambayar “Ya ake ciki?”. Zaune Smart ya kai cikin kujera dan ji yake jiri na ɗibarsa kamar zai zube a ƙasa shima. Ya dafe kansa da duka hannayensa kamar bazai cema Ahmad ɗin komai ba. Sai zuwa can ya furzar da zazzafan numfashi ya ɗan kallesa ya girgiza kansa, dai-dai nan Aunty Khadijah ta leƙo ta sake kiransa. Ta shi yay cikin ƙarfin hali ya nufi ɗakin. Batare da aunty Khadijah ta kallesa ba tace, “Kaimin ita Bathroom ka sakata a ruwan dana haɗa, ka riketa da ƙyau dan zata iya zabura”.
Duk yanda tace masan hakan yayi, sai ko gashi Lulu tai wata gigitacciyar zabura lokacin da yake sakata a ruwan. Da ƙyar ya iya rirriƙeta ajiyar zuciya mai nauyi na suɓuce masa yayinda wanin sashe na zuciyarsa ke matuƙar jin tausayinta da jin haushin kansa mai tsananin gaske. Sai da ta shafe kusan minti biyu tana fisge-fisgen kafin ta saki wani irin kuka mai tsuma zuciya tana mai ambaton sunansa da kausasashiyar muryar ta data gama ɗashewa cikin roƙo da magiyar ya barta, karya aikata. Kalamaine data dinga roƙonsa da su a lokacin da ya gaza amsa mata dan yakai fagen da bazai iya fahimtarta ba a lokacin. Goshinsa ya haɗe da nata yana ambaton, “Kiyi haƙuri Mawaddat kiyi haƙu……”
Bai kai ƙarshen kalma ta ƙarshen biyar ɗin ba ta ƙwalla wani masifaffen ƙara da zabura……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣8️⃣
………Aunty Khadijah bata ma san sanda ta afko bayin ba. Da ƙyar suka iya riƙe Lulu su biyun, alamar ya fita aunty Khadijah tai masa, badan yaso ba ya fitan ita kuma ta shiga cikin ruwan ta riƙe Lulun da jikinta ke karkarwa sosai. Ta gama fahimtar minene matsalar Lulun, ko muryar Smart ɗin bata son ji sam dan firgitata take sake yi, dan haka ta fara mata magana cikin lallashi da kulawa, sannu a hanakali yanayin nata ya shiga canjawa, ta koma laƙwas sai kuma ta saki kuka da riƙe aunty Khadijah. Cigaba da lallashinta Aunty Khadijah tai da canja mata ruwa har sai da ta tabbatar ruwan zafin yay mata ratsawar da zai iya bata nutsuwar da take buƙata sannan ta fito ta ɗaukar mata kaya. Smart na zaune ya dafe kansa bayan ya gama ƙarfin halin yaye bedsheet ɗin saman gadon ya canja da wani. Shiya ɗakko kayan ya bama aunty Khadijah ta koma bayin, babu jimawa sosai sai gata ta fito riƙe da Lulu da ke takawa da ƙyar tana hawaye. Ya nufosu da niyyar taimaka musu aunty Khadijah ta girgiza masa kai, dole yaja ya tsaya badan yaso hakan ba. Sai matsanancin tausayinta da ke ratsa shi ganin yanda take tafiyar a wahalce duk da dama rabin jikinta a jikin aunty Khadijah yake. Saman gadon ta kwantar da ita sannan ta ɗaura mata ruwan data riga ta haɗama alluran barci a ciki masu ƙarfi. Cikin sa’a ruwan baifi mintuna bakwai da fara shiga jikinta ba barci mai nauyi ya ɗauke ta, ajiyar zuciyar da take saukewa a jajjare kawai kake iya ji.
Aunty Khadijah ta sauke numfashi da ajiyar zuciya tana kallonsa, yanda ta kafesa da idanun ya sashi kasa jurewa yay ƙasa da nasa. Zama tai a bakin gadon da masa nunin ya zauna shima. Zaman yay kamar yanda ta buƙata.
“Aliyu ka kwantar da hankalinka abinda ya faru bashi bane dalilin shigarta a wannan halin.”
Da sauri ya ɗago ya kalleta, cikin nuna mamaki ya ce, “Amma aunty kafin yau ban taɓa ganinta a irin wannan yanayin ba”.
“Bazaka gantaba dama, saboda ba’ai mata abinda zai kaita ga shiga irin yanayin bane. Dan akwai ɓoyayyen al’amari a rayuwarta. Yanayin da ta tsinta kanta a ciki yayi kama da na mutanen da aka taɓa ma fyaɗe….”
“Fyaɗe!..”
Ya maimaita kalmar da wani irin yanayi mai kama da almara. Ko ruɗani.
“Tabbas fyaɗe Aliyu, shiyyasa a wannan gaɓar abinda ya faru a baya ya shiga tariyo mata kansa, dalilin da yasa ta firgita kenan har tana neman rasa tunaninta”.
Kai ya shiga girgizawa da sauri. Duk da yau ne karansa na farko da fara mu’amulantar mace bazai yarda da hakan ba. Shi mai ilimi ne, sannan mai zurfafa bincike akan abubuwan da yake buƙatar sani tun bai kai haka ba. Ya nema sani matuƙa akan mace da suffofinta. Taya ma zai yarda waninsa ya aikata abinda shi shaida ne akan zama na farko a yau ɗin nan bayan wasu awanni kaɗan. Sake girgiza kan nasa yay da janye idanunsa da ya zuba akan Mawaddat ya maida su ga Aunty Khadijah. “Aunty mudai yi wani tunanin ba wannan ba, Mawaddat she is virgin hundred percent”.
Cikin mamaki ta ce, “Aliyu kasan mi kake faɗa kuwa?”.
“Tabbas wannan shine gaskiya. Na baki kowace irin dama kuma ta tabbatarwa ta hanyar aikin ki”.
Sosai hakan ya nema saka Aunty Khadijah a ruɗani, amma kuma tabbas ta san Aliyu akan gaskiya da furtata, sannan ita kanta a yanayin data ga Mawaddat ya tabbatar mata yau ta fara sanin ɗa namiji a rayuwarta, dama tana son sake tabbatarwa ne. Miƙewa tai tsaye ta fara kaikawo kusan na minti guda, sannan ta juyo tana kallon Smart da ya sake zubama Mawaddat dake barci da sauke ajiyar zuciya har yanzu idanu. “Aliyu indai hakane kuwa akwai ɓoyayyen al’amari ƙunshe da rayuwar Mawaddat. Tunda har ka tabbatar min na yarda da kai, amma tabbas an taɓa harar rayuwarta da wannan siffar kuma lamarin bai kasance ƙarami a gareta ba, dan ta ajiyesa a zuciyarta da har takai yake iya firgitata irin haka. Ba kowa ne ake kai masa harin fyaɗe ya ke tsintar kansa a irin matsanancin firgicin nan ba har sai ya tabbata an aikata masan. Shiyyasa kaji nace maka an aikata matan da farko”.
Kansa yake jinjinawa cike da nazarin kalamanta. Tare da haɗasu waje guda da wasu ɗabi’un Lulu da mabanbanta kalamanta a wasu lokuta. Idan ya ɗauki kalamanta na safiyar yau da ta tabbatar masa zata iya halakashi kamar yanda ta kashe wancan, hakan na nufin abinda Aunty Khadijah ta faɗa tabbas dole ne ya zama gaskiya, sai dai ba’a cimmata ba. Idan aka ɗauki yanda take kallon maza, da yanda ta tsani duk wani da ya aikata fyaɗe da tsaiwar da take akan case irin hakan cikin zafi da zafafawa. Waɗan nan duk hujjojine abin kallo da dubawa. Maganar Ammah a randa ya kaita gidansu da take ce masa ya kusanta kansa da ita ya fahimci damuwarta, dan akwai ɓoyayyen al’amarin data fahimta game da ita a cikin hirarsu. Anya kuwa ma shaye-shayen yarinyar nan baida alaƙa da wannan al’amarin? “Oh my God!” ya faɗa a zahiri yana furzar da iska mai zafi.
Aunty Khadijah ta ce, “Ka kwantar da hankalinka Aliyu. Wannan damar gareka take na bincika ainahin gaskiya a yamzu. Dan inhar ta iya faɗar duk abinda ke a ranta tamkar mun yaƙi kaso sittin ne cikin ɗari na halin da take a ciki, in ba hakaba zakuyita fuskantar matsala ne kai da ita matsayin ma’aurata dan kaima zata dinga kallonka ne da wannan siffar a duk sanda ka raɓeta. Dan al’amarin ya matuƙar taɓa brain ɗinta da rayuwarta.”
“Insha ALLAH Aunty zanyi iya bakin ƙoƙarina akan hakan. Sannan ni kaina ina son sanin kowanne tsinanne ne wannan domin ɗanɗana masa fiye da azabar daya dasama ruhinta na tsawon lokaci. Sai dai ina roƙon alfarmar kar wanda yasan wannan zancen dan ALLAH”.
“Karka damu Aliyu aikina ne hakan. Akwai amana tsakanin likita da majiyaci, balle ma abinda ya shafeka muma ya shafemu. Kallon ɗaya daga cikin ahalinmu nake maka tamkar Ahmad. Haka itama Mawaddat tana da alaƙa damu mai ƙarfi. Dan haka in sha ALLAH a duk sanda kake buƙatar wani taimako ka nemeni”.
“Insha ALLAH aunty Nagode sosai, ALLAH ya saka da alkairi”.
“Amin. Sai kuma kayi haƙuri dan yanzu koda ta farka gaskiya akwai daru, dole sai ka kauda kai dan itama ba daga gareta bane tun farko an dasa mata tsoron hakanne a zuciya. Dan ma kayi matuƙar yin farar dabarar kiran Ahmad ɗin kuje asibiti, da ace kace sai har zuwa safiya brain ɗinta zai iya birkita fiye da hakan. ALLAH dai ya rufa mana asiri yay mana maganin azzaluman mutane”.
Ya amsa mata da amin zuciyarsa na masa ƙuna. Da ga haka ta ajiye masa magunguna suka fito falon inda Ahmad ke zaune cikin damuwar daɗewar tasu. Dan a ƙalla sun samu cikakkiyar awa guda a ciki. Suna fitowa ya miƙe zumbur idanunsa akan Smart. Aunty Khadijah batace masa komai ba ta nufi hanyar fita tana kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunta. Smart zaiyi magana Ahmad ɗin ya taresa da faɗin, “Please Mawashi ka gafarce ni!”.
“Akan me? Ahmad kaida ka taimakeni ka kawo min aunty Khadijah akan lokaci, ni ya kamata na nema afuwar taso ku da nai a daren nan”.
Kai Ahmad ya girgiza masa da cewa “Aliyu laifina ne, na aikata kuskure”.
Sosai ƙirjin Smart yay masifar bugawa, dan abinda Ahmad ke nufi daban shi abinda zuciyarsa ta kawo masa daban. Sai kuma yay saurin ture hakan a ransa ya zubama Ahmad ɗin idanu. “Mi kake son faɗa Ahmad, ka bani abuɗe kasan bana son kwana-kwana”.
Hannu Ahmad ya kai saman kansa ya shafa, sai kuma ya furzar da huci mai ƙarfi. “Na zuba abu a cikin FURAR nan ɗaya. Saboda ma an tabbatar min maganin nada ƙarfi yasa na saka ɗaya kawai, sai dai zuciyata taita angizani akan na ƙara ta yadda zaka kasa control ɗin kanka har sai ka tabbatar da abinda muke fata.”
Shiru kawai Smart yay yana kallon ƙasa hannayensa duka a cikin aljihun dogon wandonsa. Kamar bazaice komai ba sai kuma ya ɗago ya dubi Ahmad ɗin yay ƙaramin murmushi da sai ka ƙura masa ido zaka tabbatar yayi. “Baka jin magana Ahmad sam wlhy, ban san mi kake nufi zakai kenan ba ai da ban yarda munsha furar da ka kawo ɗin ba. Amma ka rubuta ka ajiye zan rama nima”.
Ba haka Ahmad yay zaton ji ba dan haka ya zuba masa idanu kawai yana kallonsa. Ɗauke kai Smart yay gefe da sake faɗin, “Ban san kallo malam kaje ka kai aunty Khadijah gida ta huta”.
Yanda Smart ɗin yayi duk sai Ahmad ya sake jin jikinsa yay sanyi. Sai dai dole suka fito dan dare yaja kusan ƙarfe biyu. Godiya Smart ya sakema aunty Khadijah tare da harar Ahmad da ke kallonsa har yanzu dan shi gani yake tamkar Smart ɗin ya shanye komai ne kawai a ransa dan ganin aunty Khadijah. Bayan wucewarsu ya rufe ko’ina da kashe komai. Ɗakin ya koma inda Lulu da aka sakama ƙarin ruwa take. Ya jima tsaye yana kallonta wasu abubuwa masu girma game da ita na sake hauhawar farashi a zuciya da ɓargonsa. Kafin ya lumshe idanunsa tare da ramƙwafawa kanta ya sumbaci goshinta da idanun nan da suka sha kuka yau da bakin tsiwar da ya tabbatar kona dare ɗaya ne dai ya mutu murus yau. “ALLAH yay miki albarka _Noorun Nisaaa_” ya ɗan ja sunan da hura mata iska akan idanunta yana murmushi mai sanyi ƙasan zuciyarsa cike da ɗunbin tausayinta…
Da ga haka ya miƙe ya nufi bedroom yana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Jikinsa ya tsaftace. Koda ya fito maimakon kwanciya sallaya ya shimfiɗa ya fiskanci alƙibla domin miƙa godiyarsa ga UBANGIJIN talikai mai rahama mai jin ƙai. Sai gabannin asuba da ya fuskanci ruwan daya saka mata na biyu da Aunty Khadijah ta bari ya ƙare ya je ya cire shi ma. Zama yay kawai ya saka hannunta cikin nasa ya zuba mata ido, yanda take barcin da sauke numfashi a hankali lokaci zuwa lokaci takan saki ajiyar zuciya. Abubuwa da yawa yake nazarta a kanta. Tun daga randa ya fara ganinta a airport da yaje ɗakkota har zuwa masifar da ya dinga ci a wajenta, aurensu da zaman sati uku da kwanaki huɗu yau cikon na biyar. Ya bata sunan HAWAINIYA da kan canja akowane lokaci da kuma kowane irin yanayi. Kai tsaye baka yanke mata hukunci akan kanta dan sanin ainahinta sai ALLAH. Wato duk bawan da kake kallo yana rayuwa akan kuskure ashe kai tsaye yanke masa hukunci da abinda idonka ya gani a kansa tamkar son zuciya ne. Duk wanda zai baka amsa a kanta zai ce maka she is bad girl ne kai tsaye, domin da wannan siffofin take bayyana kanta wa duniya. Dalilin shine haka aka raineta, haka ta tashi, da hakan kawai tai imani a matsayin gaskiya. “Lokaci yayi da zan san wacece ke Mawaddat? Wace irin turnuƙun ƙura kika tsallake a baya data gina miki rayuwa kamar haka? Wanene yaso lalata miki rayuwa? Miyasa mahaifinki ya nuna miki soyayya amma ya gagara tsayawa akan tarbiyyarki? Miyasa ahalinki sukai sakacin fuskantar rayuwarki na cikin wani ƙulli tun a gaɓar da ya dace ace sun fuskanta ɗin? Ina son sanin waɗan nan amsoshin da ga bakinki MATATA. na miki alƙawarin sake gina nagartacciyar rayuwar da zata fahimtar da ke tsakanin fari da baƙi koda sun gauraye a mazubi ɗaya da izinin ALLAH. In sha ALLAHU zan share miki dukkanin hawayenki na zuci dana bayyane da tafukan hannayena na maye gurbinsu da tarin farin ciki Mawaddatan’warahmah”. Motsawar da tai ya bama hannunsu damar sake matsewa cikin na juna tamkar mai jaddada masa ta amshi dukkan kalamansa itama. Hakan ya sakashi lumshe idanu da sakin ajiyar zuciya………..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣9️⃣
…….A ɓangaren Alh. Sulaiman Garko yana barin wajen Dada Alh Baita ya kira a waya. Wanda ya shaida masa yana gida yau kam bai fita ko’ina ba. Ya tabbatar masa yana buƙatar ganinsu su dukansu a daren nan dan magana ce mai muhimmanci da shi. Babu musu Alh. Baita ya amsa masa tare da bashi address ɗin inda zasu haɗu. Sannan yay kiran su Hon. Nakowa suma. Cikin abinda baifi awa ɗaya ba suka haɗu a gidan hutawar Hon. Misau dake anguwar Farawa. Tsaf ya zayyane musu komai da suka tattauna da Dada, su kansu sun girgiza da jin wannan ƙulli. Hon. Nakowa ya ce, “Wato su waɗan nan na kula makirci a cikin jininsu yake. Yanzu shima shegen Yousuf ɗin nan ashe tsagerane a haka kamar na ALLAH yana wani sim-sim da kai. To anya kuwa Isma’il bai sanar masa sirrin dake a tsakaninmu ba kuwa?”.
“Abinda nai tunani kenan yasa ni nemanku da gaggawa. Dan in har zai iya irin wannan ƙulle-ƙullen kamar haka dan kada yarinyar nan ta auri ɗaya daga cikin kai da Tajuddeen to inaji a raina wannan taƙamar da hura hanci da Isma’il keyi nada alaƙa da ya sanarma yaron nan komai kuwa. Dan haka nake ganin plan B dole ne mu canja labarin da ga Isma’il zuwa Yousuf, hakan zai bamu damar jifan tsuntsu ɗaya da dutse biyu, sannan zamufi gigita rayuwar Isma’il ɗin da haukatashi”.
“Su kuma yarinyar da yaron fa?”.
Cewar Hon. Nakowa cikin zumuɗi. Duk da Alh. Sulaiman ya fahimci inda ya dosa, amma sai bai nuna masa a fuska ba, sai ma murmushi da ya saki kai tsaye ya ce, “Wannan aikin Dada zata ƙarasa mana shi. Bayan ta ɗauke ta daga wajensa sai muje plan c akansu ita da yaron, dan dama akwai tawa da shi a ƙasa”.
Nan ma sun gamsu matuƙa. Daga haka suka cigaba d tattauna abinda ya shafesu, musamman game da sabuwar alaƙar da suke shirin sake ƙullawa akan business. Har gabannin asubahi sannan suka watse…..
__________★
Yanda Smart yaga rana haka yaga wannan dare ko sau ɗaya bai rintsa ba har akai kiran sallar asubahi. Da kyar ya iya dauriyar fita massalaci. Ana idar da salla ya dawo gidan. Inda Lulu take ya sake komawa. Har lokacin tana a yanda ya barta bata farka ba. Yana tsaka da tunanin tadata ko ya barta har sai ta tashi da kanta kira ya shigo masa a waya. Yayi mamakin ganin Coach, amma sai ya ɗaga. Jin muryar aunty Khadijah saɓanin wanda yay tunani ya sashi sauke ajiyar zuciya tare da gaisheta cikin girmamawa.
Tambayar data jeho masa akan Lulu ya sashi kallonta, sai da ya ɗan furzar da iska sannan ya bata amsa da “Har yanzu bata farka ba dai”.
“Alhamdullah to karka tada ita, inasha ALLAH ina nan zuwa yanzu nan. Dan a yanayin da take a ciki bamu da tabbacin bazata sake tashi a firgicen ba. Hakanne kuma ba’aso da ga gareta”.
Ya gamsu, dan haka yayma Aunty Khadijah godiya ya na yanke wayar. Kwanciya ya ɗanyi a kan sofar ɗakin ya faɗa duniyar tunani, hakan ya Bama barci damar dinga figarsa kaɗan-kaɗan. Tsakanin wayarsa da aunty Khadijah baifi mintuna arba’in ba sai gata tazo. Sosai yaji daɗi da ƙara jin kimar waɗan nan bayin ALLAH. Bayan sun ƙara gaisawa ya fita ya basu waje. Cikin hikima ta tada Lulu wadda ta farka a firgicen kamar yanda Aunty Khadijah tai hasashe, sai dai Alhmdllh cikin ƙwarewar aiki ta nutsar da ita, tare da taimaka mata zuwa bathroom ta sake haɗa mata ruwa mai ɗumi. Shawarar sake gasa jikinta ta bata ta fito. Lulu da komai ke dawo mata dalla-dalla batai musu ba ta shiga ruwan zafin, sai da taji ya ratsata tako ina ta sake samun nutsuwa sannan ta tsaftace kanta ta hanyar wankan tsarki da shi da kansa ya koyar da ita a cikin karatunsu duk da dai dama tanayi makamancinsa bayan period, amma ko randa ya koya matan yasha harara dan yay mata bayani dalla-dalla ne. Ji take jikinta ya mata nauyi sosai, ga tauna da ƙasusuwata keyi. Bata son tuna abinda ya faru saboda ƙunar da zuciyarta ke mata. Da taimakon aunty Khadijah tai salla, bayan ta idar ta jima zaune shiru tana nazarin tushen faruwar komai na daren jiyan. Kamar wadda aka tsikara ta miƙe da sauri dan ta manta yanayin nata. Komawa tai da sauri ta zauna tana dafe kanta ta cije lips. Ƙaramar ƙarar da tai ya saka hankalin aunty Khadijah dawowa kanta. Ta nufota da sauri tana faɗin,
“Mawaddat yi a hankali banda garaje kinji”. Bata iya cema aunty Khadijah komai ba sai hawayen da suka silalo mata masu zafi. Cikin muryarta da ke a disashe har yanzu ta ce, “Aunty dan ALLAH ina son ki kaini gida”.
“Gida kuma Mawaddat?”.
“Eh aunty, dan na tsani gidan nan da komai na cikinsa. Wlhy idan na cigaba da zama komai zai iya faruwa”.
“Ki kwantar da hankalinki Mawaddat. A cikin wannan halin da kike ai wannan gidanne yafi cancanta da ki zauna fiye da ko ina. Karki ruɗar da kanki, domin yau ɗinki tanada banbanci da jiyanki. Aliyu mijinki ne, abinda ya faru tsakaninku kuma yanada banbanci da wanda zuciyarki ke kallo a baya. Bawan ALLAHn nan tun jiya hankalinsa a tashe yake da ganin halin da kika shiga, bana jin ko rintsawa yayi a daren jiya, dan ALLAH ki sakama ranki haƙuri ku fuskanci juna wataran zakiyi alfahari da hakan”.
Kuka Lulu ta sake fashewa da shi tana mai girgiza kanta, “Aunty dan baki san miya faru bane….”
“Ba sai na sani ba Mawaddat, ki adana wannan sirrinkine. Ni dai fatana ki kwantar da hankalinki ki saurari mijinki. Aliyu mutumin kirkine fiye da yanda kike zato ko tsammani. Ke da kanki zaki bama wani labarin hakan wata rana…”
“Aunty shi azzalumi ne, macuci ba mutumin kirki ba. Kuma wlhy saina ɗan ɗana masa fiye da abinda ya ɗanɗana min, ni zai yaudara ya sakama disere tablet acikin abu na sha ya min fyaɗe. Natsanesa aunty, bana son sake ganin fuskarsa a rayuwata. Kuma wlhy sai na shayar da shi mamaki, dama sai da Dada ta faɗamin amma na kasa fahimtarta. Yayi hakane saboda yasan gobe zamu rabu. Bazan yafe masa ba, kuma a yau ɗin nan komai ma ya ƙare, ya kuma saurari abinda zai biyo baya”.
A bazata suka tsinkayi deep voice ɗinsa cikin kunnuwansu dan basu san da shigowarsa ɗakin ba. “Ni ban saka miki komai kisha domin samun biyan buƙatata ba. Sannan aure nayi kamar kowane aure mai daraja da fatan mutuwa ta raba. Amma kiyi haƙuri ki bani dama na miki bayani maybe ki fahimceni kuma ki yarda” ya ƙare maganar yana ajiye tray ɗin hannunsa mai ɗauke da kofin shayi da plate da aka saka soyayyan ƙwai.
A zafafe Lulu dake masa wani irin kallo na tsantsar tsana tace, “Har abada babu yarda a tsakaninmu. Baka da abinda zaka fahimtar da ni Munafuki, azzalumi, maƙaryaci, mayaudar…”
“Mawaddat!!”.
Aunty Khadijah ta kira sunanta cikin daka tsawa. Yayinda Smart ya lumshe idanunsa har cikin rai kalmomin guda huɗu da suka fito da ga bakinta na ratsa shi. Ƙoƙarin matsawa yay gaban gadon da kofin shayi a hannunsa yayinda aunty Khadijah ke cigaba da mata faɗa. Bai gama tabbatar da takai maƙurar tsorata da shi ba sai da yay ƙoƙarin riƙota tai wata irin zabura, sai dai azaba da rashin isashen ƙarfi ya sata kasa yin kowane irin yunƙuri face sake fashewa da kuka ta furta, “NA TSANEKA ALIYU!!”.
“INA ƘAUNARKI MAWADDATAN’WARAHMAH”. ya amsa mata da tashi disashshiyar muryarsa yana tsayawa cak, kofin shayin ya ajiye a bed side drawer duk tausayinta sai ya sake mamaye masa zuciya. So yake tai haƙuri ta kwantar da hankalinta ya jera mata kalaman yabo da jinjinar ban girma, sai dai yasan bazasuyi tasiri ba a yanzu gareta, dan haka ya tattarasu ya adana a wani killataccen sashin adana manyan sirrikansa a zuciya.
Ganin Lulu na neman sake rikice musu aunty Khadijah tace yaje falo ya jirata. Kusan mintuna biyar da fitar tasa sai gata ta fito. Kallonsa tai cike da tausayawa. “Kayi haƙuri Aliyu ba laifinta ban itama. Wlhy gaba ɗaya a ruɗe take. Dan ma a hakan fa jiya an taimaka mata da wuri shiyyasa al’amarin yazo da sauƙi. Ni yanzu ina ganin mafita ɗaya ce, ka samo wadda zasu zauna tare, sannan dole kayi haƙuri na samu ko Maman Ra’is ce (Aunty Saliha) tazo ta ƙara lallashinta. Dan yanzu ni zanje asibiti ne inada theatre. Insha ALLAH komai zai dai-daita da zarar ta daina jin raɗaɗin a ranta. Sannan ka ɗanyi nesa da itan na ɗan lokaci koda yinin yau ne haka zuwa gobe”.
“In sha ALLAHU aunty Khadijah. Nagode sosai da ƙoƙarin ki kuma”.
Sosai aunty Khadijah taji daɗin yanda ya fahimta ɗin. Yayinda tausayin Lulu ke cigaba da ratsata itama harma da shi kansa Smart ɗin. Dan yarinyar tana cikin wani yanayi ne mai ban tausayi. Bayan wucewarta ɗaki ya nufa ya canja kayansa, koda ya fito sai yay tunanin bari ya ɗan leƙata kafin ya wuce, dan gidansu yake son zuwa ya ɗakko mata Maryam ko Asma’u. Kamar zai fice sai kuma dai ya nufi ɗakin nata, ya samu tana toilet, sai books guda buyu da ya gani a saman gadon da pen. Juyawa yay ya fita saboda so yake yaje ya dawo da sauri. Maganar aunty Khadijah na cewar zatai magana da Aunty Saliha tazo yasa shi bai rufe gidan ba, dan yasan sun fisu kusa da nan zata iya yiwuwa ta iso kafin shi ya dawo.. Da’ace bawa yasan gaibu ko abinda zai iya faruwa a bayansa da Smart bazai yi wannan fitar ba. Da bai bar ƙofar gidansa a buɗe ba. Da ya bari har aunty Saliha ta iso kafin ya tafi…….✍️
*_Tofa masu karatu. Mizai faru? Mike shirin faruwa? Amsoshin na a FURAR DANƘO book 2 in sha ALLAHU 👌_*
_Kumin afuwa wannan karon rubutun duk yazo a yanayi na shiririta sai dai godiyar ALLAH. Yau da gobe kenan dan na fiku son naga na kammala gaba ɗaya😭. Amma in sha ALLAH muna gab da hutawa baki ɗaya. Zamu koma part 2 ne dan in numbers na nisa rubutun gundurata yakeyi wlhy🤦. Amma insha ALLAHU zamu ƙarƙare akan lokaci._*
_Akwai ƙura fa ta gaske a book 2, dan duk wani abinda muke san sani na ƙunshe ne a cikinsa. Kudai kuyi addu’a ALLAH yasa mu koma pages goma goma mu kammala a kwana goma. Kun san fa ina matuƙar son goma😂😂._
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Furar Danko Book 2
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣
*_UK (LONDON)_*
……..Kwance yake rai-rai a madaidaicin gadon nasa da mutanen Nigeria ke kira da 6-by-6. Sai dai wannan yaji katifa mai shegen laushi da bedsheet fari tas shima mai laushin gaske da ko’a ido ka kalla zaka shaida hakan. Yanda yake ɗan furzar da numfashi sama-sama da huttai ga zufa da tai ma jikinsa jagab zai tabbatar maka da ga training ya fito. Dan wandone na jc ƙarami da ya tsaya masa a fin rabin cinya da rigarsa. Sai takalma da aka san ƴan ƙwallo da su a ƙafarsa. Jikinsa ne a saman gadon ƙafafun zube a ƙasa. Iska mai nauyi ya sake furzarwa tare da buɗe idanunsa da launinsu ke a surke. Sam babu fara’a a tare da shi, dan fuskar nan ɗam take fiye da yanda kowa ya sanshi da rashin walwala acan baya….
Cikin kuzari da ke nuna cikakkiyar lafiyar gangar jiki ya tashi zaune da ƙyau, ƙaramin tsaki ya ja tare da yamutse fuska ya fara saɓule takalman ƙafar tasa. Anan ya zubesu tare da miƙewa gaba ɗayansa ya kama rigar jikinsa ya cire cikin kamar yanayin jin haushi ya jefar da rigar ƙasa. Dogon glass ɗin da ya kasance kamar bango guda a haɗaɗɗen bedroom ɗin nasa ya nufa. Ya kai hannu ya danna wani ɗan maɓalli green. A hankali glass ɗin ya shiga raba kansa biyu har ya bada ƙofa. Shiga yay nan ma kamar a ɗan fusace, lafiyayyen toilet ne ya bayyana da ni kaina na zama baƙauya a kallo, kai tsaye ƙarƙashin shower ya nufa ya sakarma kansa ruwa yana mai jan wata nannauyar ajiyar zuciya…
*_Aliyu Mika’il Idris Mawashi_* kenan da ke amsa sunan _Smart Mawashi_ a duniyar ƙwallon ƙafa. Duk da dai kwata-kwata watanninsa uku kenan da dawowa ƙasar ta UK a London yay signing a club ɗin Queen City. Du da kasancewar ƙaramin club ne muna fatan ya zame masa wani tsanin kaiwa inda ba’ai zato ba. A yanzu Smart da muka sani na baya mai shiru-shiru da rashin sakewa da jama’a ya sake zarce hakan. Dan yanzu ba shiru-shiru ba, har miskilanci ma ya koyo. Hakan kuma ta faru ne a sakamakon faruwar shuɗaɗɗun abubuwan da suka faru a cikin watanni ukun nan da suka wuce. A gaɓar da tafi kowace gaɓa muhimmanci a tarihin rayuwarsa. A lokacin da ya gama shiryawa da tsarawa kansa gina rayuwa mai ban sha’awa da birgewa tare da matarsa. A lokacin da yay shirin ɗaukar dukkan yarda da amanar kansa data rayuwarsa domin damƙa mata. Sai labarin ya canja da ga yanda ya rubuta shi a zuciya zuwa rubutun ƙaddara.. Matarsa ta kufce masa a yayinda da burinsa na zama ɗaya da ga cikin ƴan ƙwallo a wata ƙasa ya cika. A hankali komai ya dinga dawo masa a zuciya dalla-dalla tamkar a yanzu ne yake faruwa. _(Bayan fitarsa gida a waccan ranar ya nufi gidansu cike da damuwar halin da ya jefa Lulu a ciki. Ya samu Asma’u taje aikan da Ammah tai mata gidan Aunty Bilkisu. Sai Maryam kawai da Ammah. Ko zaman kirki baiyi ba a daddafe suka gaisa da mahaifiyar tasa ya sanar mata yazo ɗaukar ɗaya daga cikin su Maryam ne dan Mawaddat babu lafiya. Hankalin Ammah ya tashi, ko neman Abba bata tsaya yi ba tace ya ɗauki Maryam suje idan Abban ya dawo zata sanar masa, dan ita a nata zaton ko ciki Lulun ta samu. Cikin sauri Maryam ta kimtsa tare da ɗibar kunun gyaɗar da sukayi domin tafiya da shi can su karya dan itama ko karyawar basu yi ba. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso kasancewar safiya ce babu yawan go slow a hanya. Sai dai me tun a yanayin da sukaga ƙofar falon a buɗe da littafin da ya gani ɗazu a saman gadon Lulu yashe a ƙofar shiga falon alamar an yarda bisa kuskure gabansa ya faɗi. Amma sai ya dake cikin ƙarfin hali suka shiga, a falo Maryam ta zauna shi kuma ya nufi bedroom ɗinsa yana faɗa mata taje ɗakin Lulun yana zuwa. Maryam ta amsa masa da to, yayinda shi kuma ya nufi ɗakin nasa. Bai wani jima ba sai gashi ya fito. Ɗan turus ya tsaya ganin Maryam kamar a ruɗe tana kai kawo. “K lafiya? Ba canai ki shigaba ina zuwa”. Da sauri Maryam ta juyo gareshi tana bashi amsa da “Yaya ai Auntyn bata nan ciki fa. Har toilet na leƙa babu kowa a ciki, hakama kitchen, sai dai duk an harmutsa wadrobe ɗinta an ɗiba kaya harma da akwati guda da aka bari kamar sauri ya hana a ɗauka”. Wani irin duka ƙirjinsa ya dinga yi, sai kuma ya nufi ɗakin da sauri shima. Kamar yanda Maryam ɗin ta sanar masa haka ya gani, sai dai shi nashi idon ya ƙara masa ganin duk wani abu mai amfani a ɗakin ma babu shi. Ƙafafunsa ne suka fara rawa, sai dai cikin dakewa ya cigaba da ƙarfafa kansa. Takardar da idonsa ya sauka kanta a bisa gado ya ƙarasa ya ɗauka. *_Na tsaneka Aliyu, bana son sake ganinka a rayuwata, amma kaje na barka da ALLAH azzalumi. Ashe wa’azin naka duk na yaudara ne kaima baka aiki da shi. Ka manta da ni har abada, dan ko’a hanya nai maka tazara irin ta sama da ƙasa, gabas da yamma. Idan ka wahal da kanka a nemana kai ka so, dan babu wanda ya isa sakani sake zama da kai koda Uncle Yousuf ne._* jiyay jiri na nan ɗibarsa yay saurin kaiwa zaune yana ambaton sunan ALLAH. Ya jima a wajen zaune kansa na yamutsa masa har Maryam ta gaji da jira ta shigo ɗakin. Hankalinta ya tashi da ganin yanda Yayan nasu ya birkice cikin ƙanƙanin lokaci. Kansa tai tana ƙwala masa kira amma sai ya ɗaga mata hannu da ƴar tsawa-tsawa yace ta fita ta bashi waje. Ta tsorata dan haka ta fita da sauri. Kamar an saita batafi minti ɗaya da fita falo cikin ɗaurewar kai ba sai ga kiran Ahmad ya shigo mata. Da sauri ta ɗaya ta kai kunneta. Ko gaisawar kirki bata tsaya sunyi ba ta shiga faɗa masa abinda ke faruwa. Gaban Ahmad ya shiga faɗuwa shima da ga can, cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi a gidan. Tambayar duniya Smart yaƙi cemasa komai har sai da ya nuna fusata sanan a taƙaice ya ce masa, “Tabar gidan”. Duk da abin ya daki zuciyar Ahmad ɗin. Sai ya shiga kwantar masa da hankali akan yana zuwa ya tabbatar bazata wuce gida ta tafi ba. Wayar Uncle Yousuf yay kira, da ƙyar ya samu ta shiga. Bayan ya gaishesa bai wani tsaya kwana-kwana ba ya sanar masa halin da ake ciki. Hakan ya ɗan ɗimauta Uncle Yousuf ɗin shima amma sai ya yanke kiran yace yana zuwa. Gidansa ya fara kira Aunty Saliha dake tsaye itama cikin tashin hankali ta ɗaga wayar da sauri. Dan dama nemansa take tun ɗazun ta gagara samunsa. Kafin ma yay mata tasa tambayar ita ta jeho masa abinda ke bakinta. “Abban Ra’is wlhy akwai matsala babba. Yanzu nan Khadijah tai kirana akan na shirya naje gidan Mawaddat babu lafiya na lallasheta da kwantar mata da hankali, banyi ƙasa a gwiwa ba nai shiri dan na shiga tashin hankalin bayanin Khadijahn. Sai dai muna kan hanya sai ga text massege ɗin ta ya shigo wai karmu nemeta, dan tayi nesa damu, na faɗa maka a kira Aliyu ya bata sakinta ta arziƙi inba haka ba zata sashi ya bada ta wuya. Duk da saƙon ya bani mamaki nacema driver yay sauri mu tafi gidan nata. lokacin da muke shiga street ɗin mun haɗu da wata baƙar mota mai tinted glass suka wuce muka wuce. Mun samu gidan buɗe da wani makwafcinsu tsaye a bakin gate ɗin, driver na ƙoƙarin shiga ya dakatar da mu cewar aiko baijin gidan nan da kowa. Dan yanzu yaga wata mata ta rirriƙo matar gidan tana kuka sun shiga mota sannan a loda akwatina a Hilux ma, shima ganin sun bar gidan buɗe ne ya sashi fahimtar babu lafiya, shine fa naketa nemanka ka kira Aliyu koka turo min Number sa amma na kasa smaunka”. “Innalillahi wa-inna ilaihiraji’un” Uncle Yousuf ya shiga maimaitawa. Nan ɗin ma baice komai ba ya yanke kiran. Mommy ya kira, itama bai tsaya sun gaisa da ƙyau ba ya jeho mata tambayar ko Lulu taje gidan. Da mamaki tace bata zo ba gaskiya, kuma batajin zatazo ɗin, dan yau tanada Shari’a. Jin haka Uncle Yousuf ya ɗan samu nutsuwa ya yanke kiran. Ahmad yay kira yace su maza court dan tana can zai turo Aunty Saliha yanzu su riƙeta. Da sauri Ahmad ya miƙe, shima Smart sai ya miƙe. Har Maryam basu bariba suka kulle gidan. Sai dai me koda suka isa can ɗin ma babu Lulu, an kuma basu tabbacin bata zo ba. Sosai yanzu kuma hankalinsu ya fara tashi, dan kowa yasan duk rintsi fa Lulu akaran kanta bazatai sakaci da aikinta ba, musamman idan akai la’akari da yanda take matuƙar son al’amarin. Sai dai yanda aka ɗibi kaya yayin barinta gidan na hargitsa ma kowa lissafi. Gidan ƴan uwa da duk aka san zata iya nufa aka fara bubbuga waya, gidan Alhaji Garko ne farko, amma sai cikin tashin hankali Dada tace batazo ba, ba cikin Kano ba har wajen Kano amma dai amsa ɗaya ce Lulu fa bataje ba. Tun kowa na ɗaukar al’amarin wasa harya fara shan hankali, zuwa yamma dole aka shigar da report police station. ALLAH sarki Smart, yini guda baici komai ba sai ruwa, dolene a kallo ɗaya ya baka tausayi, sai da Coach ya tsaresa bayan sallar magrib yasha shayi, yana gamawa kuma sai amai, sai zazzaɓi mai zafi. Dole ranar Ahmad da Abdull na gidansu sai anan suka kwana, dan suma dai tuni sun san mike faruwa Ammah duk kawaicinta a ranar sai da ta taka gidan Smart da ga ita har Abbah. Umma kam wani shegen daɗi takeji, dan a ganin ta in har wani abu ya samu Lulu iyayenta sai sun ɗaure Smart na tsawon rayuwa.
Al’amarin kamar wasa tuni ƙaramar magana ta zama babba, dan kwana ɗai-ɗai har uku babu labarin Lulu Daddy da Uncle Yousuf tuni sun wancalakar da ayyukan gabansu sun dawo Nigeria. Hakama su twins duk suna Kano. Smart yay wata irin zabgewa, bawan ALLAHn ko murmushi baka gani a fuskarsa, ya duƙufa kawai gayama UBANGIJI, dama Abba ya kai islamiyya da masallatai a taya addu’a, hakama ƴan sanda nata faman kai kawo da bincike. A cikon kwana na biyar ne fa Addu’a bata faɗuwa ƙasa a banza sai ga binciken ƴan sanda ya fara maida akalarsa kan Dada, ba komai ya kawo hakan ba kuwa sai dalilin ganin sanda aka fita da Lulu da maƙwaftansu yayi, dan ƴan sanda basu barshi ya hutaba shima. Yana ganin Dada yace ma ƴan sanda “A’a to ai wannan Maman ce na gani da yarinyar a waccan ranar, tare da wani saurayi haka mai ɗan kammani da su”. A take kowa ya dubi Dada da duk ta daburce, sai kuma ta hau borin kunya. Ran kowa a wajen sai da ya ɓaci idan ka cire Alh. Sulaiman da Tajuddeen da suka san komai. Smart kam wani irin kallo yakema Dada kawai, ji yake yau da ace bata da alaƙa da Lulu wlhy duk da tsufanta sai ya koyama matarnan hankali, dan sai ta tabbatar da ainahin Aliyu Hydar. Daddy ma dai da duk ya zabge a tsaye harda ciwo akan ɓatan Lulun a wani irin rikice yake kallon Dada da Alh. Sulaiman a karo na farko, shikam dama ya zargi Alh. Sulaiman, sai dai Uncle Yousuf ya kwaɓesa akan hakan. ALLAH sarki Uncle Yousuf sarkin dattako, da ya fahimci faɗan na cikin gidane sai ya sallami ƴan sandan kawai, da ƙyar suka tafi dan sun ce dolene Dada ta fuskanci shari’a. To abinka da manyan mutane, a take akai kiran cp ya basu umarnin tafiya. Bayan wucewarsu ne fa gida ya hargitse, dan Dada tace bazata taɓa faɗar ina Lulu take ba sai Smart ya saketa. Karan farko da tun faruwar al’amarin ya saki wani shegen murmushi mai ƙona zuciya a baɗini mai kuma hasala abokin gaba a zahiri……..✍️
_Alhamdullah barkanmu da sake dawowa a book 2. Yanda muka fara a Sa’a ALLAH yasa mu kammala da nasarori. Ina godiya da jirana da kukayi tare da fatan alkairi 😘😘👏._
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣
……..Iyayensa ya kalla cikin nutsuwar data ratsashi a yanzu najin tabbacin ina matar tasa yake, cike da girmamawa ya ce, “Abba ku tashi muje gida kawai”. Abba da tausayin ɗan nasa ya ƙara mamaye masa zuciya ya ce, “Aliy ba tafiya gida ne masalaha ba, ka bari dai a sasanta muji miye dalilin aikata hakan”. “Abba bata da wani dalili face na son zuciya. Ina son cigaba da ganin girmanta a matsayinta na uwa kamar yanda kuka tarbiyantar dani girmama kowace irin furfura, tun farko ma ita ya kamata na zarga, amma banyi hakan ba saboda shi zargi bashi da amfani. Sai dai amsa ɗaya zan bada a yanzu har gaban Abada *_BAZAN SAKI MAWADDAT BA_*. Sai dai ayi ɗayan biyu. Ko na MUTU tamun TAKABA, ko ni na mata wanka na sallaceta zuwa kabarinta. Wannan dalilan guda biyu ne kawai zasu iya raba wannan auren da izinin ALLAH!!”. Ba su Dada ba hatta Abbah da Ammah sai da Smart ya girgizasu, dan magana yake a dake, a fusace, a kuma kausashe, hatta da Ahmad dake a matsayin aboki zai iya rantsewa bai taɓa sanin Smart ɗin yanada irin wannan zafin ba. Harara Dada ta watsa masa da faɗin, “Oh burinka kenan dama ta mutu kaci gadon dukiya. Sheɗani to ALLAH ya fika, sakin Mawaddat kuwa idan bakai ta arziƙi ba zakayi ta wuya dan bazamu taɓa haɗa zuria da jinin tsiya jinin talauci ba. dama koda ka aureta ai asiri kai ma iyayen nata matsiyaci”. Murmushi Smart ya saki da taɓe bakinsa cikin halin ko’in kula da zancen Dada. Sai ma ƙoƙarin barin falon da yake yi batare da ya bata amsa ba . Alh. Sulaiman da ya kai maƙura a kan Smart ɗinne ya miƙe a fusace yana nunashi da yatsa. Sai dai kafin ma yace wani abu Smart ya nunashi shima cikin gargaɗi, “Kai! Karka kuskura shiga ramin da zai bizne rayuwarka ta har abada ya barka da gangar jiki kawai da idanun kallo. Sunanka ƙanin uwa ne ba uba ko ƙanin uba ba. Ni da kake gani na nan Sulaiman na fika fiye da abinda ka iya wlhy. Idan kace zaka saka ƙafar wasa da ni sai na gigita rayuwarka ta yanda kai a karan kanka bazaka taɓa morarta ba balle waninka. Magana ake ta mutane ba irinku riɓɓaɓu ba okay…” da ga haka Smart ya sa kai yay ficewarsa kafin ma Alh. Sulaiman da jikinsa ke rawar ɓacin rai dana firgita ya iya furta komai, da gaskiyar Lulu idanun Smart sun cancanci kowane irin suna, musamman a yau da ransa ke a ɓace dan Alh Sulaiman idanun Smart na ɗaya da ga cikin abinda ya razana shi. Fitar Smart ɗin ta saka falon zama tsit, yayinda Alh. Sulaiman ke nuna ƙofa cikin rawar baki data hannu. Daddy ya sauke wata irin gajiyayyar ajiyar zuciya a karo na farko, sai kawai yaji hawaye sun cika masa ido, dan tunda Smart ya fara magana yake kallonsa harya fice. Uncle Yousuf ne ya tashi yabi bayan Smart, haka ma Ammah da Abbah. A gate suka sami Smart yana waya da Coach, dan a gobe ya kamata ya wuce dama, sai dai da yayi aniyar haƙura dan bazai iya tafiya wata ƙasa batare da anga Lulu ba. Amma a yanzu ya gama yanke shawarar wucewa babu fashi. Uncle Yousuf da ke kallonsa da murmushi yay masa nuni ya shiga mota inda Abba da Ammah suke, bai musa ba ya shiga. Har gida Uncle Yousuf ya kaisu, inda ya samu zama na musamman da Abba da Ammah. Shi ya lallashesu akan su kwantar da hankalinsu dan ALLAH a zubama su Dada ido aga gudun ruwansu, dan ya tabbatar sun aikata haka ne dan Alhaji Garko baya nan. Sosai Abbah ya gamsu da bayanin Uncle Yousuf ɗari bisa ɗari tare da ganin shawarar itace dai-dai. Bayan wucewar Uncle Yousuf Abba da Ammah suka sake zaunar da Smart sukai masa nasihar ya cigaba da shirinsa na tafiya kawai kamar yanda Uncle Yousuf ya faɗa da masa faɗan abinda yay ma Alh. Sulaiman da Dada. Haƙuri ya basu da alƙawarin bazai sake ba. Wannan shine sanadin tattara al’amarin Lulu ya haɗa kayansa a washe gari shi da Uncle Yousuf da Coach suka nufo ƙasar UK a London. Inda yay signing da wani ƙaramin team Queen City. Su Uncle Yousuf sun sake masa nasiha akan ya kwantar da hankalinsa kan al’amarin da kanta zata bijirema su Dada. Shi dai cikin dauriya da dakiya yake amsa musu da to kawai. Amma a cikin ransa shi kaɗai yasan irin ƙunar da yake ji da matuƙar kewar matarsa. Sai dai ƴan mazan sun ɗauki aniyar da jarumtar a wannan karon na sai ya tabbatar ma family ɗin Lulu gaba ɗaya da ita kanta shi ɗan halak ne, sannan talauci ba hauka bane ba. Duk da dai yanayin yaso taɓa shi da son maidashi sanyi-sanyi a watanni ukun daya samu kansa, sannan sam yanzu baka ganin fara’a a fuskar Smart, ya sake zama shiru-shiru a yanzu ma harda miskilanci zamu iya cewa ya ƙaro. Dan bai shiga sabgar kowa, abinda ya kawosa kawai yake yi sai bautar ALLAH. Baya zuwa ko ina da ga gida sai idan yana buƙatar sayen wani abu ya ɗan fita ya sayo ya dawo sai wajen training ɗinsu. Burinsa shine ya manta da komai kamar yanda Uncle Yousuf a koda yaushe ke bashi shawara, dan har yanzu Dada taƙi faɗin inda ta kai Lulu. Duk da yanda aka so yin ɓatacciya tsakanin Daddy da Alh. Sulaiman, dan Daddy yana ragama Dada kodan darajar sunan uwa, amma tunda ya fahimci da haɗin bakin Alh. Sulaiman akai komai sai hankalinsa yay masifar tashi, yasa a nemo masa Smart, Uncle Yousuf da ke nuna shi al’amarin bai damesa ba a zahirin dan yana son Daddy ya maganantu a wannan karon yace masa ai baya ƙasar. Zancen ya girgiza Daddy duk da bai san ina Smart ɗin yaje ba ko abinda ya tafi yi. Da ga baya ma sai Dada ta tattara ta bar ƙasar itama zuwa jiyyar mijinta….)
Wannan shine abinda ya faru kafin tahowar Smart England.
Ɗaure da guntun towel ya fito a ƙugu, sai ƙarami yana tsane jikinsa da sumarsa da ya jiƙe da ruwa. Mai ya shafa sama-sama tare da shiryawa ciki ƙaramin wando da riga armless. Gadon nasa ya sake hayewa yay kwanciyarsa dan barci yake ji sosai. Sai dai kafin barcin ya ɗaukesa tunani ya jasa tsahon lokaci….
Wannan kenan.
____________________★
*_CANADA_*
Amai take sosai cikin galabaita da fitar hayyaci, a kallo ɗaya zaka fahimci yanda duk jikinta ya saki sai huttai take da ƙyar. Cikin tausayawa mai aikin da suka taho tare tun daga Nigeria ta ke jera mata sannu. Bayan ta gama aman ruwa ta sakarma kanta daga inda take zaune tana hawaye. Haka take tun can da ma bata da juriyar ciwo, a yanzu kuma da take jin ciwon tamkar ya bambanta da duk wanda ta sabayi ne ke sake galabaitar da ita da raunana mata zuciya, har tana jin anya bazata bijirema kakar tata ba ta bayyana kanta kota koma gida Nigeria. Tsahon watanni uku kenan da barowarta gida Nigeria bisa taimakon kakarta Dada. _(Dan a waccan ranar bayan fitar Smart da ga gidan ta fito toilet da taje yin fitsari, duk da tai masa kurarin barin gidan ba’a ranar tai niyyar hakan ba, sannan batai niyyar sanarma wani nata abinda yay matan ba kamar yanda aunty Khadijah ta bata shawara. Saman gado ta koma ta ɗauki book nata da take adana muhimman sirrikanta ta fara rubutu tana hawaye, bata kai ƙarshe ba ya cika dan haka ta buɗe sabo ta cigaba. Tana tsaka da rubutun ne taji sallamar Dada a bazata, kafin ma ta farga har ta shigo bedroom ɗin nata kai tsaye. Hawayen da Dada ta gani a fuskarta ya sata nuna tashin hankali da fara jera mata tambaya, sai taji zuciyarta ta ƙara karaya ta sakarma Dadan kuka kawai. Komai Dada bata tsaya tambayarta ba ta hau haɗa mata kaya, bayan ta kammala drivern da ya kawota ya shigo har ciki ya dinga kwasar kayan, yana kammalawa ita kuma ta ce Lulu ta tashi suje, da farko Lulu taso tirjewa akan ta bari Aliyu ya dawo, amma Dada ta balbale ta da masifa. Dole badan taso ba tabi umarninta ta sako. Sai dai tanayin taku biyu uku Dada ta rabga uban salati da antayo ashariya mai kawuna bakwai ta dire. Balbale Lulu tai da masifa irin wadda bata taɓa mata ba, tare da tambayoyi masu tsaurin gaske da suka saka Lulun ɗan jin nauyi harta gagara cewa komai. Sai da taga ta takura mata tace faɗuwa tayi. Hakan ya ƙara harzuƙa Dada ta fisgeta suka fita, sai dai zafin da take ɗan ji ya sata tirjewa dole Dada ta kamata suka fita cikin lallaɓawa. Anan ne makwafcinsu ya gansu, sai dai ita Lulu bama tasan maƙwafcin nasu bane ba. Lulu ta roƙi Dada suje Court akan case ɗin yarinyar nan da take so a ƙarƙare a yau, inda suka samu alƙali suka juye masa kuɗaɗe akan ya cigaba da riƙe mata mutumin a gidan yari zata bar ƙasar dan bata da lafiya. Da ga court hanyar airport suka ɗauka, suna isa basufi minti arba’in da biyar ba jirgin zuwa Abuja ya shirya tashi, dama Dada tasa a tanada mata ticket tun barowarsu gida. Ita kaɗai ta wuce Abuja Dada ta koma gida. Maimakon gidan Uncle ɗinta Khamil wata mata ce tazo ta tareta, tasan matar tare da Dada da daɗewa, suna kiranta Hajiya Shuwa. A ranar gaba ɗaya ta yini kwance ne da zazzaɓi a gidan Hajiya Shuwa, hakama washe gari dai duk gata nan ne dai babu isashen lafiya tare da ita. A kwana na uku Dada tai kiranta a waya ta tsara mata zance cewar ai Aliyu na nan nata zaginta da cewar wai ta tafi yawon banza ne, dan haka sun saka ƴan sanda sun kamashi a yanzu haka ma kotu zasu kaisa ya bata takardar sakinta. Ran Lulu ya ɓaci matuƙa dajin wai Smart na zaginta har da dangantata da karuwa, dan haka tacema Dada tana son ƴan sandan nan su ƙara wajiga rayuwasa kuma ya saketa. Kwana biyu bayannan da ke zama biyar da barowarta Dada ta kirata nan ma ta sanar mata Aliyu wai ya saketa. Duk da abinda take fata ke nan sai taji wani iri, daga ƙarshe ma ranar yini tai babu lafiya zuciyarta a cunkushe. A ranar ta sanarma Dada tana so tabar Nigeria zuwa America, amma sai Dadan ta bata shawarar taje gidanta na Canada tunda babu wanda yasan da shi, dan Uncle Yousuf yay ikirarin ɗaukarta da kansa ya maida gidan Aliyu ko tana suma tana mutuwa ne. Ran Lulu ya sake ɓaci, ta kuma sake jin ƙwarin gwiwar nisantar ahalinta baki ɗaya. Wannan shine dalilin tahowarta Canada tare da mai aikin da aka haɗota da ita mai suna Ummita. Sai dai tunda sukazo zuciyarta taƙi nutsuwa waje ɗaya, abubuwa da yawa tsakaninta da Smart a ɗan zamansu sun zame mata barazana a barci da ido biyu, wannan ya sata sake buɗe babin shaye-shayen ta sosai-sosai. Ko abinci bai dameta ba da ga shaye-shaye sai barci. A kwanakin da bazasu wuce sati biyun nan ba ne abubuwa suka fara canjawa, idan tasha kayan shaye-shayen ta tana kammalawa zatai amansu, tun tana ɗaukar al’amarin wasa har takai bata son warin kowane irin ƙwayar magani, amma cikin ƙarfin hali take daurewa ta sake gwada sha, ta kuma sake aman nasu. Wannan dalilin ya sata ɗaga ƙafa kwana biyu, sai kuma hankalinta ya fara dawowa jikinta har salla da lokaci yayi kamar wadda aka zabura sai ta tashi tayi. Kwana uku da suka wuce kuma sai zazzaɓi ciwon kai da kasala, ga yawan mafarkin Aliyu kamar wani magic a gareta. Sai duk randa tai mafarkin nashi takan tashi da ɓacin rai har taji buƙatar shan kayanta ko zata manta da shi. Sai kuma dai ta daure taƙi sha dan ko tunawa tai da su sai taji amai. Yau kuwa wayar gari tai cikin wata irin damuwa da kewar wani abu data kasa canka a ranta, sai zuciyarta daketa faman ƙuntata, cikin son kauda yanayin ne ta samu ƙwaya tasha amma ta rantse bata zama a cikinta shine take amayar da ita a yanzu)………✍️
Wannan kenan.
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣
…….Dole da taimakon Ummita mai aikin nata ta gyara jikinta ta kamota ta fito da ita bedroom. Cikin wando dogo da sweater ta shirya tare da Safa mai kauri sosai, ta haye gadon cikin rawar ɗari taja bargo har saman kanta. Tare da bama Ummita umarnin ƙara mata gudun room hitter ɗin ɗakin. Dan wani irin rawar sanyi take har haƙoranta na haɗuwa waje guda. Ga hawaye sun gagara tsayawa (yau fa an taɓo manyan mata🤣🙏).
Yanayin da Lulu ke ciki ya tada hankalin Ummita, number da suke waya da Dada jefi-jefi ta lalubo ta kira, kamar baza’a ɗagaba ma sai kuma aka ɗaga, cikin ladabi Ummita tai sallama da gaida Dada, daga can ta amsa a gadarance da tambayar ina Lulu. Cike da damuwa Ummita ta sanar mata gata kwance babu lafiya, dama kusan kwanakin nan haka take ganinta sama-sama, sai dai rashin tabbatarwa yasa bata faɗa mata ba sai yau. Rai a ɓace Dada ta shiga zagin Ummita ɗin, duk ta rikice dan tana bala’in son Lulu, zamu iya cewa soyayyar mahaifiyarta ce ta dawo kanta. Ita dai Ummita haƙuri kawai take bama Dada kawai. Dan ta tabbatar masifar tsohuwar original ce.
Ba’a rufa mintina goma da katse wayar Dada ba alerm ɗin gidan ya kaɗa, miƙewa Ummita da ke falo tai ta nufi ƙofar, bata buɗe ba kai tsaye ba, ta danna numbers dake jikin ƴar computer ɗin kusa da ƙofar dake manne a bango dan ganin wanene. Baturiyar mace ce tsaye, cikin nuna alamar tana ganin Ummitan da ga wajen itama ta ce, “Hy” cikin ɗaga hannu. Amsa mata Ummita tai itama da “Hy” ɗin. Cikin murmushi matar ta cigaba da magana cikin harshen nasara. “Sunana Doctor Olivia, Nazo nan ne bisa umarnin Mrs Garko”. Yanda ta kira kalmar Garko ɗin taso bama Ummita dariya, amma ta dake da ƙyar sai murmushi da tai mata tare da ɓuɗe ƙofar. Sun sake gaisawa da Dr Olivia, Sannan tai mata rakkiya ɗakin da Lulu ke kwance.
Ganin yanda jikin Lulu yay zafi sosai yasa Dr Olivia cewa dole suje asibiti, a take tai kiran ambulance cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gasu. Lulu na rawar sanyi da faɗin su barta ita bazataje ko ina ba su Dr Olivia suka ɗauketa a ambulance ɗin tare da Ummita suka wuce. Suna zuwa babu ɓata lokaci aka shiga da Lulu ciki tare da rufuwa bata gudunmawar gaggawa.
*_UK_*
Hankalin Dada da ke jiyyar mijinta ya tashi sosai, amma tanata ƙoƙarin dakewa dan kar Alhaji Garko da ya fara samun sauƙin jikinsa Alhmdllh ya fahimta tare da sauran yaransu da sukan zo dubashi. Idan wannan tawaga ta wuce sai wata kuma tazo, abinka da masu hannu da shuni, kallon fita ƙasar ake kamar barin Kano a shiga Katsina ne. Alhaji Garko da bai san halin da ake ciki ba har yanzu dan babu wanda ya sanar masa saboda halin da yake ciki ya zubama matar tasa ido cikin tausayawa, dan shi ya fassara yanayin nata ne da gajiyawa musamman da yake akwai tsufa. Cike da kulawa ya ce, “Hajarah kina buƙatar hutu, ya kamata kije gida haka nan tunda jikina da sauƙi nima, har ma muna sa ran sallama nan da ƙarshen watannan”.
“Haba dai Alhaji ya hankalina zai kwanta kana nan ina can, duk da dai jikinka Alhmdllh amma har yanzu kana buƙatar kulawa. Danni ko sallamarka sukayi bana son ka koma gida Nigeria yanzu har sai ka sake hutawa anan magana ta gaskiya.”
Murmushi yay irin nasu na manya da faɗin, “Hajarah rigima kenan. Yanzu ni da abubuwa ke jirana tari-tari tunda ALLAH yasa da sauran kwanana a gaba mizai sa na kuma sake sabon zama anan ai gara na koma gida ko?”.
“Humm Alhaji wlhy wannan gaskiya ce ba rigima ba. Gara dai ka sake hutawa dan muna komawa can hayaniya ma ta isheka musamman ta ƴan siyasar nan da ba gajiya suke ba. Dan haka dan ALLAH ka yarda kawai sai ka sake hutawa, nima yanzu inaga maimakon tafiya Nigeria bari na ɗan je Canada na huta na kwana biyu kafin a sallamekan ko.”
Ɗan jimm yay na alamar tunani, sai kuma cikin nuna fahimta ya ce, “Shike nan idan hakan kike so uwar garke na. Yanzu yaushe zaki wuce Canadan?”.
“Eh to ko zuwa yamma haka tunda ga su Khamil da iyalansa nan sun iso ko, auta ma yace min zai baro Saudiyya shi da matarsa gobe in sha ALLAH. Kaga dai ai ka sake samun masu kulawa”.
Murmushi yay mata cikin nuna gamsuwa. Dan Dada kam a wajen bama miji kulawa jaruma ce, tsaye take kan abinta ta kankane ko ina tunda ƙuruciya har girma babu wata mace data taɓa raɓar mata miji da sunan kishi. Wannan tsananin kishin nata yasa hatta matan ƴaƴanta take jin kishinsu akan ƴaƴan nata da suma take matuƙar so da ƙauna tamkar ubansu. Babu ɓata lokaci ta hau shirin wucewa Canada, dan ji take kamar ta rufe ido ta isa taga hanlin da ƴar jikarta take a ciki, saboda a nata bahagon tunani babu abinda zuciyarta ke raya mata sai kodai Smart, ko Uncle Yousuf wani ya sakema Mawaddat asiri ne.
Dai-dai lokacin da Lulu ke cika awanni goma sha ɗaya a asibitin su Dr Olivia Dada ke isowa ƙasar ta Canada. Tunda ƙuruciya an riga da an san lungu da saƙo na ko’ina, dan a duk ƙasar da suke yawan zama suna da gidansu na kansu musamman manyan ƙasashen nan masu ji da kansu irinsu England, America, France Chaina, Saudiyya, Dubai, dan da gasken gaske wannan family sunada dukiya, bayan wadda mahaifinsu ya gada a wajen nasa mahaifin ya kuma tara nasa na kansa, su kansu yaran kowanne ba ƙyalan bane wajen kuɗin, dan babu wanda ke zaune kaf ɗinsu a neman na kansu suke. Ko marigayiya Mawaddat mahaifiyar Lulu data kasance mace ɗaya tilo a cikinsu sanda tana raye tsaye take akan neman na kanta saboda haka aka gina musu rayuwa, duk da yana da dukiya kuma ya gada ne shima a wajen mahaifinsa bai yarda yaransa su zama cima zaune ba, suna ayyuka a cikin gwamnatin ƙasarsu da na wasu ƙasashe, suna kuma Business ƴaƴa da iyaye har ma da jikoki. Cab ta ɗauka tun daga airport zuwa asibiti kai tsaye, dan a ƙage take da son ganin halin da jikar tata ke ciki. Wadda har yanzu ana kan tafka rigima akan ɓoyetan da tai dan bayan ita sai Alh. Sulaiman kawai suka san ina Lulun take. Hatta da Tajuddeen sunƙi sanar masa. Ita Dada zuciyarta ɗaya ce game da ɓoye Mawaddat dan kawai ta rabata da Smart ne matsayinsa na talaka jikanta Tajuddeen ya samu. Yayinda shi Alh. Sulaiman ba haka kawai bane a tashi zuciyar, dan a yanzu haka bai fara aiwatar da plan ɗinsa bane akan Lulun sakamakon rasa inda Smart yake da yay shi kuma. Dan tun washe garin da Smart ya baro 9ja yasa malami binciko masa shi amma ƙasa ko sama babu labarinsa. Amsa ɗaya suke samu a bincikensu shine ya ɓoye kansa dan kar ya saki Lulu. Duk da dai suna zargi Uncle Yousuf ne ya ɓoyesa amma a ɗan tsukunnan sun ƙara tsananta bincike kasancewar har yanzu basu sami wani point ba akan hakan. Dan shi Uncle Yousuf ɗin ma ya sake baro Nigeria ɗin zuwa harkokinsa da ya bari bayan yayma Daddy tas da tabbatar masa da cewar ya zare hannunsa akan al’amarin Lulu, dan ya fahimci goyon bayan da Daddyn ke batane a baya ya bata lasisin biyema Dada tabar gidan aurenta. Saboda ya tabbar da babu haɗin kan Lulu Dada bazata taɓa iya ɗauketa a gidan aurenta ba harta ɓoyeta gashi ana neman wata uku kamar wasa.
*_NIGERIA_*
Sosai Daddy yana cikin wani hali na azabtuwar zuciya game da abubuwa da yawa. Na farko shine ɗan uwansa dake fushi da shi. Ƙaunar da yakema Yousuf a zuciyarsa daban ce a wannan duniyar, dan zai iya rantsuwa ko ƴaƴansa baya musu irin wannan ƙaunar har Lulun da ake kallo ya fifita. Na biyu rashin sanin inda Lulu take har yanzu, tun yana ɗaukar al’amarin wasa Dada zata dawo da ita bayan wasu kwanaki har lamarin ya fara bashi tsoro. Lokacin da yaje UK duba Baba Garko har roƙonta yay akan tayi haƙuri Lulu ta koma gida koda bazata koma gidan mijin ba, dan tabar aikinta da mutane ke matuƙar buƙatarta. Amma sai Dada ta murje idanu tai masa tas dole yaja bakinsa yay shiru dan yana ɗaga mata ƙafa kodan darajar sunan uwa da take amsawa. Sannan fa Daddy dama can Uncle Yousuf ya fishi zafi, shi dai barsa da zuciyar tsiya kamar ɗan kuturu. Abu na uku wani salon rainin wayo da Alh. Sulaiman ya ɗan fara kawo masa da nuna shi yanzu a shirye yake da shi akan komai, sai zuciyarsa ta fara bashi anya kuwa bada haɗin kan Alh. Sulaiman ɗin Dada ta ɗauke Lulu ba kamar yanda yay zargi tun farko. Idan ko haka ne to tabbas a wannan karon ya shirya duk wacce ma za’ai ayi shima. Wannan tunanin ne ya zaburar da shi yau daga gida daya fito yace driver ya wuce da shi office ɗin Alh. Sulaiman Sufi Garko. Sanda suka iso ma shi bai kai ga isowar ba, dan haka sukai zaman jiransa. Baifi mintina bakwai ba a tsakani sai gashi shima. Sai da ya shiga da kusan mintina huɗu drivern Daddy ya shiga ya nema musu iso. Alh. Sulaiman da tun shigowar Daddy cikin Companyn aka sanar masa, yana shigowa kuma ya shaida motarsa yay wata dariyar mugunta da bama sakatariyarsa umarnin shigo da shi.
Tunda Daddy ya shigo Alh. Sulaiman da yay wata kishingiɗar iskanci a kujera yana jujjuya kansa ya saki murmushi mai ma’anoni da yawa. Yi Daddy yay kamar bai gansa ba, sai ma ya kai zaune duk da ba’a bashi damar hakan ba. “Ina fatan kana lafiya?”. Daddy ya faɗa a takaice. A gatsine Alh. Sulaiman ya amsa masa da “A office ka sameni ai ba’a gadon asibiti ba”.
“Kuma haka” cewar Daddy a gatsine shima. Batare da ya jira cewar Alh. Sulaiman ɗin ba ya cigaba da faɗin, “Sulaiman ina kuka kai min yarinyata?”.
“Ka shirya ganinta yanzu kenan?”.
Idanu Daddy ya tsurama Alh. Sulaiman cikin ɓacin rai, sai dai kafin yace wani abu Alh. Sulaiman ɗin ya ƙyalƙyale da wata dariyar mugunta yana miƙewa tsaye. Takowa yay inda Daddy yake ya ja kujerar dake kallon wadda yake zaune shima ya zauna tare da ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya. Fuska ya tsuke ya zubama Daddy dake kallonsa cike da tsana idanunsa shima. “Isma’il Ibrahim Jiƙamshi! A da kana ɗaukar duk zantukana matsayin kurari ko? Kana tunanin bazan iya illata rayuwar Mawaddat ba dan kawai tana ɗiyar ƙanwata?. To kayi kuskuren sanin waye ni, dan zamanka da ni na tsawon shekaru bakwai bai maka amfanin komai ba kuwa. Bari kaji wlhy wlhy da ace na san da wannan sirrin a hannun Mawaddat ƙanwata kafin mutuwarta, ni da hannuna zan kasheta bayan na amsa, sai ALLAH ya taimaketa ta mutu a karan kanta kafin na sani ɗin, amma duk da haka bata tsiraba ta barma ƴarta gadon laifinta. Dan haka Isma’il ina maka gargaɗi na ƙarshe, ka bani camara ɗin nan, ka kuma saka a ranka baka taɓa sanina ba har abada, in ba hakaba, a wannan karon saina wargaza rayuwar kaf family ɗinka bata Mawaddat kawai ba. Dan haka zaɓi ya rage naka….”
Murmushi Daddy yay mai ma’anoni da yawa duk da yasan duk abinda Alh. Sulaiman ɗin ya faɗa zai aikata fiye da hakan. Amma cikin nuna halin ko in kula idonsa akansa kyam ya ce, “Sulaiman kenan. Ka manta ni Isma’il ɗin wanene nima. Sannan banda haukarka a tunaninka baka camara na nufin gogewar abinda ka tafka da in kaf family naka sukaji sai sun maka tsanar da sai ka gwammaci mutuwa da rayuwa. To idan ka manta bari na tuna maka, bayan abinda Mawaddat ta ɗauka nima ai nasan komai, ko toshewar basirar taka takai ka manta cewar komai na sani tunda da bakinka ka kirani ka sanarmin abinda kayi kuma na gani da idona, hasalima tare dani ka ɗauki yarinyar ka kai ƙasan gotter ka jefar. ai ba abinda Mawaddat ta ɗauka bane kawai hujjar. Sannan na biyu Sulaiman kada ka manta a tafin hannuna kuke kai da su Alh. Baita, idan yanzu na sanarma duniya su waye ku a ƙasar nan wlhy wlhy ba dukiya ko matsayi ba sai anyi faca-faca da namanku da taimakon mahaifinka dan kafi kowa sanin irin tsanar da yay ma abinda kuke aikatawar. Ai dama na sanar maka tun a waccan ranar, sai na ɗan ɗana ma zuciyarka rayuwa cikin fargaba da zullumi fiye da yanda ƙanwarka ta ɗanɗana min a tsahon shekara ɗaya dana rayu da ita…..”
“Nima ai na tabbatar maka sai dai mu rayu a tare cikin zullumin da fargabar ko ka manta”. Alh. Sulaiman ya faɗa a zafafe cikin katse Daddy. Sai kuma ya ƙyalƙyale da dariya da faɗin, “Isma’il kenan a tunaninka kaima ban san a yanda ka rayun bane, ko cakake ban san kaima kana rayuwa bane cikin irin yanda kake tunanin ka sani a tsahon waɗan nan shekarun. Ka gaya min inba tsoro ba miyyasa ka ɗauke ƴarka daga Nigeria da ga randa na tabbatar maka saina hukunta rayuwarta bisa laifin mahaifiyarta? Miyasa kaketa kaffa-kaffa da ita fiye da sauran ƴaƴanka?. Amsar itace Tsoro ne! Kana jin tsorona Isma’il!! Hhhhh tabbas wannan tsorone!!”.
Da ƙarfi Daddy ya buga decks tare da miƙewa a zafafe………✍️
Tofa fagen na manya ne yau🚴🚴🚴
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣
…….“Kai ɗin banza da zanji tsoronka Sulaiman. Ka sannni kaima ai, ni na wuce maka kanwar lasa, sannan ni ƙadangaren bakin tulune a rayuwarka data abokanka ta yanda kuka rasa yanda zakuyi dani. Ƙarshen target ɗinku shine ku kasheni dai, kuma na tabbatar muku a randa kuka kasheni wlhy ko minti ɗaya bazan cika ba da ɗaukewar numfashi kuma duniya zatai muku zafin da sai kun gwammace mutuwa kamar ni, dan sai mutanen duniyar sun san suwaye ku. Idan ba tsoro kuke ji ba miyya hanaku aikatawar a tsahon shekarun nan. Miyasa kuka kasa bayan kunada kowacce irin dama? Miyasa baku aikata bane sulaiman? Ku kashenin mana? Maza ku kashenin idan kun cika ku tsagerane dan ALLAH!!”.
Matuƙar razana Alh. Sulaiman yayi da kalaman Daddy, cikin ɓacin rai da zafafuwar zuciya ya nunashi da yatsa lips ɗinsa na rawa. “Haka kace ko?”.
“Haka nace Sulaiman, idan kuma bakaji ba na sake maimaita maka. Kuma wlhy na baka daga nan zuwa ƙanƙanin lokaci ɗiyata ta dawo gareni inba hakaba sai na sakaka nadama irin wadda sai ka gammaci mutuwa da rayuwa. Dan duk inda kasa ƙafa ka sani ni Isma’il ƙaddararka biye nake da kai. Plan ɗinku na gaba shine sakama Yousuf cocaine a kaya yayinda da zai baro ƙasar Chaina zuwa Nigeria. Bance ku fasaba dan ALLAH, amma ku sani wannan shine mabuɗin farko na kiran mutuwarku. Ni Isma’il kallon kitse kukema rogo kawai, dan ko poisining ɗin Baba da kukayi na barku ne kawai bisa wani dalilina na tarkon dana ɗanama rayuwarku. FURAR DANƘO NAKE, A SHEKARA ANA DAMU BANI FARAU-FARAU. Mawaddat kuwa bazan sake cemaka ina take ba, in dai har ita ɗin jinina ce da kanta zata maido kanta gida bisa bigiren bijire muku. Ku muje zuwa wasan a yanzu na shirya masa….”
Har Daddy yabar office ɗin Alh. Sulaiman da yay sumar tsaye bai iya dawowa a hayyacinsa ba. Sai da Daddyn yay banging ƙofar ne ya zabura wata zufa na feso masa a illahirin jikinsa. Bai ma san sanda ya since hular kansa ya hau fifita da ita ba jikinsa ma wata irin rawar shiga ruɗani da tashin hankali. Ji yake kamar mafarki yakeyi, shin Isma’il da ya sani ne haka wai shin ko canja shi ankayina? wagga al’amari haka kamar a mahwalki. Shiy yasan Isma’il nada zuciya kam tabbas batun yanzu ba, amma bai taɓa tabbatar da zai iya wani yunƙuri ba bayan kafiyar daya sanshi da ita kawai musamman da yaga tunda suka fara ƴar tsamar nan Daddyn nayi tamkar yana shakkarsa a koda yaushe, lallai ya yarda bakatsinan mutum abin tsorone yau. Da ƙarfi ya hankaɗa kayan saman table ɗin nasa da nuna ƙofa a kausashe ya furta “Isma’il You really are playing with fire!!!….”
(😂Daddy ni kaina ka shayar dani mamaki, ashe jinin katsinawan dai na aiki a jininka)
*_CANADA_*
Sosai hankalin Dada ya sake tashi ganin yanda Lulun tai wani masifar ɗashewa ta ƙara haske sosai, ga komai nata ya ciko musamman ƙirjinta. Dan ma zazzaɓin daya tasota gaba ya ɗan saka jikin nata girgiza ƙasa kaɗan kwana biyun nan. Tambaya bayan tambaya Dada ta shiga jeroma Dr Olivia akan mike damun jikar tata haka. Kai tsaye Dr Olivia ta sanar mata Lulu na ɗauke da ciki wata uku da kwanaki biyu. Tamkar an fasa irin ƙaton dutsen nan mai girgiza yanki da gidajen wajen gaba ɗaya haka maganar Dr Olivia taima Dada saukar aradu a tsakkiyar ka. Cikin razani da zabura ta maimaita kalmar “Ciki!” ɗin zuciyarta na bugawa. Dr Olivia ta sake tabbatar mata da hakane. Wata muguwar ashariya Dada ta lailayo ta dire akan Smart. Tare da faɗin, “ALLAH ya tsinema wannan shegen yaro dangin talauci dangin jaraba. Yanzu nan sai da dai ya ɗirka mata ciki. Amma Mawaddat kema ƴar banzar yarinya ce. Randa na ɗakkoki da ga gidan yaron nan har tambaya naita jera miki akan yanayin dana ganki amma kikace min faɗuwa kikayi ashe-ashe miƙa masa jiki kikai ya lalube”. Sai ga hawaye suna cika idon tsohuwar nan dan ɗaurama kai masifa. Kasancewar da Hausa Dada tai maganar duk sai hankalin Dr Olivia ya tashi ta shiga tambayarta ko lafiya. Rai ɓace Dada tace mata ba komai tana zuwa. Cikin rawar jiki ta fito tana neman lambar Alh. Sulaiman ɗanta…
*_LONDON_*
Iya ƙoƙari yana yi wajen ganin ya ajiye matsalolinsa gefe ya fuskanci rayuwarsa ta yanzu da cigaban da ya riskeshi. Sai dai hakan ya gagara matuƙa duk da akoda yaushe yay waya da Ammah ko Abbah ko Uncle Yousuf da Coach shawara suke bashi akan ya dai ƙara daurewa. Ammah kan masa nasiha mai ratsa jiki da tabbatar masa in sha ALLAH komai zai zama labari, kuma in har Mawaddat matar da zai rayu da itace duk abinda za’ai sai ta dawo garesa. Wannan ƙwarin gwiwar da mahaifiyarsa ke bashi kan ƙara ƙarfafa masa gwiwa. Sai dai hakan bai hanashi kasancewa cikin mafarkin Lulu ba a duk sanda zai kai kwance da sunan barci. Al’amarin ma har yana neman zame masa jiki akoda yaushe a koda yaushe cikin wanka yake. Ya kasa manta dare mafi daraja da muhimmanci da ya zama wani babban jigo a cikin zamansu na kwanaki ashirin da shidda. Tunashi kansa yay murmushi ko ƙaramar dariya harma da tausayawa. Duk da ashi kansa yasan darene da bazai iya tantance komai yanda ya kamata ba illa dai yasan a shi kansa yasha wahala balle ita. Amma sambatunta ko neman agaji zai ce na wannan dare ya kasa manta komai.
Yau ma kamar kullum cikin shiri fita wajen training ya fito daga dogon ginin estate ɗin da masaukinsa yake zaune mai hawa kusan ɗari da hamsin, a hawa na tamanin da biyar yake dan haka ya sakko ta lifter har zuwa block A, sanye yake cikin dogon wando na sport da riga mai dogon hannu itama dai irin wandon ce. Sosai ya canja gaba ɗayansa tamkar wanda dama tun farko yake rayuwa anan ɗin. Fatarsa ta sake gogewa ya sake yin haske da kwarjini da cikar kamala a cikin wata uku kacal tamkar wani baƙin bature. Yawan training da sukeyi ya sake buɗe masa halittun gaɓɓai da sake kasancewar sa tsayayyen mutum da za’a iya kallo a jarumi. Kunnensa manne yake da bluetooth yana magana a hankali kamar baya so alamar waya yake amsawa. Ba kowa bane face Ahmad da yay kiransa, duk da yanayin da yake a yanzu na sake zama shiru-shiru da rashin son magana idan Ahmad ɗin yay kiransa yakan ɗan sake suyi hira. Da ɗan gudu-gudu ya fara tafiya jefi-jefi yakan ɗagama wanda suke ɗan wucewa kamar shi a hanya hannu. Yayinda yake cigaba da magana da Ahmad ɗin. Da ga estate ɗin nasu zuwa inda suke training ɗin akwai ƴar tazara sai dai ba wata mai yawa ba sosai, amma duk da haka yakan jure tafiya a ƙafa koma cikin ɗan gudu-gudu kamar yanda yake yi a yanzu domin fara motsa jininsa kafin ya isa. Hakan na ƙara masa ƙarfi da zaburarwa a yayin da ya shiga fili sai karsashinsa ya ƙaru. Sosai sabon baturen Coach ɗin nasu ke yaba ƙwazonsa da jin cewar za’a mori yaron matuƙa idan aka ƙara tsayawa akan al’amarin sa zai zama babbar kaddara, shiyyasa akoda yaushe yake sake jan Smart a jikinsa da ƙara masa dabaru kala-kala dan Smart irin mutanen nan ne masu shiga ran mutane a komai nasu, ga shi baida hayaniya sam, yanayin da yake ciki ma ya sake maida shi miskili a yanzu duk da hakan ba halinsa bane a baya. Amma hakan bai hanashi zama abin so ga wasu ba hatta a cikin teammate ɗin nashi. Alhamdullah yana ƙoƙarin maida hankali tare da ajiye gyambon dake mamaye a zuciyarsa gefe domin fuskantar abinda yaje yi a yanzu, wannan ne karo na farko da zai tunkari babban wasa link na ƙasar da za’a fara, Yana alfahari da hakan duk da team ɗin nashi ƙarami ne. Cikin zafin nama ya iso inda sauran team mate ɗinsa suke. Babu ɓata lokaci suka shiga abinda ya tarasu, sosai yake nuna ƙwazo dake firgita al’amarin wasu a cikin abokan nashi bisa dalilai masu yawa. Na farko shi kaɗaine baƙar fata ɗan Africa a cikinsu, na biyu musulmi, na uku baƙon da har yanzu bai wuce watanni uku da kwanaki ba a cikinsu, amma yana taka leda da sunan training mai firgita zuciya. Ga yanda Coach ɗin nasu yay masifar maida hankalinsa kansa a ɗan ƙanƙanin lokaci na basu mamaki. Yau ɗin ma dai mamakin daya saba basu ya basun, dan har aka tashi babu alamun gajiyawar raunin jiki dana gaɓɓai a tattare da shi. Sai dai su a zahirine kawai suke ganin haka, shi a karan kansa can ƙasan zuciyarsa cike take da rauni. Ga wani irin faɗuwar gaba da ya tashi da ita yau tamkar wanda wani mummunan abu ke neman faruwa da shi. Amma yanayinsa na dakewa da rashin walwala yasa sam su basu fahimci komai ba.
Cikin huttai ɗai-ɗai irin na wanda yasha kai kawo ya samu waje ya kai zaune yana kwankwaɗar ruwan dake hannunsa. Sharkaf yake da zufa tamkar wanda yay wanka. Yanda yake shan ruwan kai a sama ya bama Adams apple ɗinsa damar motsawa cikin kaikawo haɗiyar ruwan da sauri-sauri. Sai da ya shanye ruwan tas ya sauke bottle ɗin yana furzar da nannauyar numfashi. A hankali ya zame jikin kujerar ya kwantar da bayansa yana mai lumshe idanunsa da kai hannunsa saman ƙirjinsa dai-dai zuciyarsa dake cigaba da bugawa ya dafe yana karanto addu’a da fatan koma minene ke tunkarosa ALLAH ya sauƙaƙa masa shi ya kuma bashi juriyar ɗauka…..
*_NIGERIA_*
Alh Sulaiman na tsaka da kai-kawon tashin hankalin abinda ya faru tsakaninsa da Daddy kiran Dada ya shigo masa. Kasancewar wayar a hannunsa take yana son kiran Hon. Nakowa yaja ɗan tsaki. Kamar zai share kiran mahaifiyar tasa sai kuma dai ya ɗaga tare da kaiwa kunnensa batare da ko ya gaisheta ba a daƙile ya ce, “Dada ina ɗan wani uziri yanzu idan na kammala zan kiraki”.
Da sauri Dada ta ce, “Sulaiman muna cikin tashin hankali ka tsaya muyi magana dan wannan ma uziri ne babba”. Ɗan tsammm ya dakata da ga yunƙurin yanke kiran da yay yace “Uhumm” alamar saurarenta. Cikin rawar muryar ɓacin rai da tsufa Dada ta cigaba da faɗin, “Sulaiman ina Canada yanzu haka. Yarinyar nan dake tare da Mawaddat ce tai kirana wai gata babu lafiya tanata amai. Na ɗauka kawai normal fever ne nai kiran Dr Olivia ta dubata, amma sai ta kirani tana faɗa min zasu wuce da ita asibiti dan jikin yay zafi sosai. Hankali tashe na taho bayan nama Babanku dibara. Daga airport asibin kawai na is…..”
Cikin ƙosawa Alh. Sulaiman ya tare Dada da faɗin, “Dada bar wannan dogon bayanin kawai faɗi mike damunta?”.
“Wai tana da ciki har na wata uku”.
“What! To ubanwa yay mata shi?”.
“Sulaiman wazai mata banda ɗan iskan yaron nan”.
Wata irin zafafaffiyar iska Alh. Sulaiman ya furzar ransa na ƙara dagulewa. Batare da wani tunani ba murya a kausashe ya ce “Zubar da shi za’ai Dada. Ki haɗani da Dr Olivia ɗin muyi magana”.
Ɗari bisa ɗari Dada ta amince da maganar ɗan nata, dan dama itama wannan shine a ranta. Alh. Sulaiman yay magana da Dr Olivia sun kuma gama ƙarƙare komai akan zubda cikin jikin Lulu kafin ma ta dawo hayyacinta tasan da shi. A wajen bature wannan ba komai bane ba, amma sai dai Dr Olivia ta tabbatar masa sai sunyi gwaje-gwajen da ya dace kafin cire cikin bawai zasuyi kai tsaye bane kamar yanda yake so shi. Yana yanke wayar Dr Olivia ta shiga yin abinda ya dace game da abinda zasuyi kan zubda cikin na Lulu ta hanyar gwada ƙarfin jininta da wasu abubuwa irin nasu na likitoci da su kaɗai suka san su………✍️
🚴🚴🚴🚴uhhhmmm bazance komai ba nidai.
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣
……..Basuyi mata allurar zubda cikin ba kamar yanda Alh. Sulaiman da Dada suka bada umarni har Lulu ta farka, an gama dai duk wani shirye-shirye har Dada ta saka hannu. A hankali ta buɗe idanunta da sukai mata nauyi sosai tana bin ɗakin da kallo, sai da hankalinta ya gama dawowa jikinta sannan ta fahimci a asibiti take. Yunƙurawa tai da niyyar tashi sai hakan yay dai-dai da shigowar Dada ɗakin. “Sunahanallahi Mawaddat kin tashi?” cewar Dada tana nufota. Ita ta taimaka mata ta ƙarasa tashi, tare da kaiwa zaune a kusa da ita. Hakan ya bama Lulu damar kwantar da kanta a jikin Dadan tana hawaye. “Yaushe kika zo?”. Ta tambaya cikin raunin murya irin ta mara lafiya. Cike da kulawa Dada ta sake rungumeta a jikinta da faɗin, “Tun ɗazun dear. Ya kike jin jikin naki yanzu haka?”.
“Dada ko ina namun ciwo, ga yunwa ina ji sosai”.
“Ba dole kiji yunwa ba kina ɗauke da jinin yunwa. Shegen yaro da bai wuce saiti abu yi guda ya ɗiraka miki ƙunshi ya barki da jidali”.
Da mamaki Lulu ta ɗago ta dubi Dada saboda rasa gane ina zantukanta suka nufa. Dada ta ƙyaɓe baki cikin hasala tana yin ƙwafa. “Dada wai mi kike faɗi ne?”.
“Mtsoww ba komai tashi muje na kaiki ki wanke baki kizo kici abincin”. Duk da Lulu na son jin fassaran zantukan na Dada sai batai musu ba ta tashi a jikin nata, da taimakonta ta wanko bakinta da fuskarta suka dawo. Apple da tace tana so ta bata ta sha, takai kusan rabi ta ajiye ta ce ta bata yugut. Shi tasha sosai dan kaɗan ta rage a babbar robar da yake ciki. Sosai Dada ta saki baki tana kallon Lulun kamar wadda ke’a cikin yunwa. Ɗan gumin da ya tsatstsafo mata na ƙoshi ta kai hannu ta share tare da komawa jikin Dada ta lafe. Shigowar Dr Olivia ya sakata miƙewa zaune. Sannu Dr Olivia ke mata cikin fara’a da jin daɗin ganin ta tashi da daɗin rai, bayan ta ɗan tsokanarta ta ciro allurar da zatai mata. Lulu bata wani damu ba, dan ta ɗauka normal allura ce, dan haka babu musu ta yarda akai mata doctor na cigaba da tsokanarta.
Minti talatin dai-dai dayin allurar nan wani irin ciwon mara na azaba ya tasoma Lulu. A take jikinta ya fara vibration, tai wani irin dunƙulewa waje guda tana kiran “Wayyo ALLAH na Dada marata”. Yanda ta saki siririyar ƙararar sai da zuciyar Dada ta harba, hankali tashe tai amfani da wayar landline dake a ɗakin tai kiran doctor Olivia. Tamkar dama a kusa take babu jimawa sai gata ta faɗo, zuwa sannan jini ya ɓalena Lulu abin babu daɗin gani….
Iya wahala da azaba Lulu ta Shashi, inda da ƙyar aka samu jinin ya tsaya, akai mata allurar barci tare da gyarata, barcin wahala ne ya ɗauketa sai wata irin tagwayen ajiyar zuciya take saukewa a cikin barcin. Dada da duk ta shiga damuwa ta shiga tambayar doctor yanda ake ciki, Doctor ta tabbatar mata da aiki yayi ƙyau, dan yanzu haka dai ciki ya fita sai kuma ɗan jiyyar jiki da Lulun zatai na kwana biyu. Wata irin ajiyar zuciya mai nauyin gaske Dada ta sauke, a take tai kiran Alh. Sulaiman, a lokacin yana tare da su Hon. Misau suna tattauna batun Daddy. Kamar yaƙi ɗauka sai kuma dai ya ɗaga yana kaiwa kunne. A ɗan daƙile ya ce, “Dada nafa sanar miki inada uziri, mi kuma ya faru yanzun?”.
A ɗan ɗokance da ture maganarsa ta farko Dada ta ce, “Ai an kammala aiki yanzu haka ciki yabi gottern turawa kuma”. Ajiyar zuciya Alh. Sulaiman yayi da faɗin, “To maddala, na san zasu sallameku yau ku koma gida, zuwa anjima idan na samu nutsuwa zan kiraki”. Daga haka ya yanke wayar batare da ya jira tace wani abu ba. Hakan ya bama Dada haushi dan bata gama maganarta ba, amma sai batace komai ba bayan jan tsoki. Kamar yanda ya faɗa zuwa dare da Lulu ta sake farkawa aka sallamesu. Duk da Lulu najin jikinta cikin rashin ƙarfi kwata-kwata ga jiri na ɗinarta bata kawo komai a ranta ba. An basu magunguna suka hau cab zuwa gida. Sun samu Ummita ta gama gyara ko’ina sai tashin fresheners masu ƙamshi da gidan keyi, cikin ƙarfin hali Lulu ta ce ma Dada tana son tai wanka first, amma ta taimaka mata. Dada da kanta ta cuccuɗa Lulu tare da taimaka mata suka fito, kaya ma da taimakonta ta saka, tana gama sawa tasha tea ɗin da mai aikinta Ummita ta haɗa mata bisa umarnin Dada. Sosai ta sha shayin har ma abin yaso bama Dada mamaki, ita dai cikin sauke numfashi ta koma ta kwanta dan barci takeji har yanzun.
*_BAYAN KWANA UKU_*
Yau kawani uku kenan da zubar da cikin jikin Lulu da batasan da shi ba ba kuma tasan an zubar ba. Ta ɗan ƙarasa jiyyarta ta kwanaki biyu yayinda Dada ke kula da ita a duk motsinta. Yanda ta miƙe da wuri zai baka tabbacin zuwan Dada yay mata daɗi, dan akoda yaushe tana nane da ita. Duk da tana jin kewar ƴan gidansu musamman Daddy, Uncle Yousuf, Da Ammah sai take ƙoƙarin dakewa da sakama ranta haushinsu akan basa sonta. Ga kuma Dada a kaikaice tana sake cusa mata laifinsu hadda sharri. A duk sanda kuma Dada ta ɗakko zancen Smart sai Lulu taja tsaki da yamutsa fuska cikin shagwaɓa tacema Dada bata son ji, ita a daina mata koda zancensa. Hakan nama Dada daɗi da sake zaburar da ita cusa ma Lulu ƙiyayyar Smart a zuciya har ma da su Uncle Yousuf. Tun ma abin baya tasiri a ran Lulu har ya fara a randa take cika kwanaki biyar da samun lafiya a bazata sai ga Alh. Sulaiman da Tajuddeen. Lokacin tana kwance a falo tana kallo. A zahiri ta warke ragal. Sai dai tana jin wani irin kasala da son shan fruits, dan rigima ma yau sai cewa tai a mata kunun gyaɗa. Da Dada tace ina za’a samo wata gyaɗa anan sai ta sanya musu kuka na gaske. Dole Dada tai kiran wani saurayi ɗan ƙawarta da suma suke nan Canada ɗin amma asalinsu ƴan Nigeria ne ya bazama nemawa Lulu gyaɗa. Sai ko gashi ya samo, Ummita ta amsa ta haɗa mata kunun data buƙata sannan aka samu lafiya. Wannan kunu shine a gabanta har zuwa yanzu lokaci-lokaci takan zuba tasha abinta har sai taji yakai mata sannan ta ajiye. Sororo tai da ganin Uncle ɗin nata da Tajuddeen, dan ita dai ganin nasu yazo mata a bazata. Yanayinta babu yabo babu fallasa ta tashi zaune tana musu sannu da zuwa. Sai kuma ta ɗan dubi Tajuddeen a yatsune tare da balla masa hararar kallon ƙurillar da taga yana mata. Sanye take da doguwar riga kalar ja da tabi jikinta ta lafe, sai rigar sanyi data ajiye gefenta kasancewar gidan akwai hitter dake ɗumama ko’ina. Rigar ta fisga ta sanya tare da komawa kwancenta kamar yanda take da. Sai dai ta danna wani ɗan maɓalli dake gefen kujerar ya bada ƙara sai ga Ummita da sauri ta fito da ga wani ɗaki tana faɗin, “Aunty kina buƙatar wani abu n…” ta kasa ƙarasawa saboda ganin baƙi. Batare da Lulu ta kalleta ba ta ce, “Ki sanarma Dada anyi baƙi”. Ummita data zube tana gaida su Tajuddeen ta amsa da to tana miƙewa ta nufi ɗakin da Dada da Lulun ke kwana.
Ta wutsiyar ido Alh. Sulaiman ke kallon Lulu da nazartar ta, ba yau ya fara fahimtar girman kai da izzar yarinyar ba irin ta uwarta da ma shegen ubanta ce. Dan duk da yake amsa sunan yayan mahaifiyarta bata wani sakewa da shi, hasalima a duk sanda suka haɗu takan dinga acting like tana jin haushinsa. Hakan yasa yake zargin ko mahaigunta ya sanar mata wani abu a kansa ne. Wata ƴar ƙaramar ƙwafa yayi ciki-ciki a ransa yana faɗin (Zan dawo dake cikin hankalinki ai yarinyabke da ubanki dama duk mai daure miki ƙugu). Tajuddeen kam kai tsaye ya kafe Lulu da kallo, itako duk da tana jin idanunsa a kanta tai biris da shi tamkar bama tasan ALLAH yay zamansa a falon ba da ga shi har ubansan. Laifin Tajuddeen ne ya shafi mahaifinsa Alh. Sulaiman a wajen Lulu, dan bama shi ba, duk wasu ƴan gidan su Tajuddeen Lulu ta tsanesu a dalilin Tajuddeen ɗin ba kamar yanda shi Alh. Sulaiman ke tunanin Daddy ya faɗama Lulun sirrinsa bane.
Cikin nuna mamaki Dada dake fitowa ta ce, “A’a wai dama da gaske ne kuna tafen ashe dai?”.
Murmushi Alh. Sulaiman yayi da amsa ma mahaifiyar tasa da “Wlhy kuwa Dada ai na tabbatar miki babu abinda zai hanamu zuwa. Idan muka gaisheki sai mu wuce mu duba Baba kuma duk da shi Tajuddeen zai dawo nan Canada ɗinne akwai aikin da zaiyi”. Dada bata samu damar bama ɗan nata amsa ba saboda miƙewar da jikanta yay Tajuddeen yaje ya rungumeta. Lulu da duk ke saurarensu gabanta ya faɗi jin wai Tajuddeen yazo aiki ne nan Canada. To lallai dolene kam tabar ƙasar nan kenan a wannan gaɓar. Dan bataga haɗin kifi da kaska ba tsakaninta da Tajuddeen bazasu taɓa kasancewa a inuwa guda ba. Tsam ta miƙe cike da izzar nan tata sai dai rashin ƙarfin jiki na ciwo duk ya cinyeta a tsaye ta ɗauki flaks ɗin kunun gyaɗarta ta bar falon. Su duka da kallo suka bita kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa. Dada ta katse shirun da faɗin, “Bara yarinyar nan ta shirya muku abinci ko. Sannunku da hanya”.
Bakin Tajuddeen a washe yana sauke nannauyar ajiyar zuciya da ga dawowa hayyacin bin kallon Lulu da yay da ido ya kalli kakar tasu. Ido ya kashe mata tare da mata nuni da ɗakin da Lulu ta shiga da baki. Dada tai ƙaramar dariya da faɗin, “To Alhaji zumuɗinka kadai bi komai a hankali, dan bamu san wane kalar barbaɗe shegen yaron nan yay mata ba, maybe bata gama dawowa cikin hankalinta ba ta kuma butsare mana a karo na biyu kadai san halin taurin kai irin na Mawaddat da shegen fitina”.
“Karki damu Grandma, komai zai tafi dai-dai kamar yanda aka tsarashi. Indai ni ne a wannan gaɓar babu garaje. Bamma san tasan komai har sai an ɗaura auren”.
Ƙaramar dariya Dada tayi, yayinda Alh. Sulaiman ya kura musa ido kawai, sai dai baice dasu komai ba…….✍️
_🤔To an taɓa aure akan aurene? Yau naga lukutar masifa Dada da Alh. Tsule fa babu man kai zasu iya ɗaurawa…🚴🚴🚴_
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣
……..Lulu bata sake fitowa falon ba tana a ɗaki, sai in lokacin sallah yayi ta tashi tayi, dan tunda ta dawo asibitin nan kuma sai hankalinta ya dawo jikinta sosai. Da lokacin sallah yayi kamar wadda ake zabura sai Smart yazo mata a rai, miƙewa take cikin jan ƙaramin tsaki da son kauda al’amarin sa tai sallarta. Alhamdullah game da shan kayan shaye-shayen ta ma tunda suka dawo asibitin tamkar wadda aka tsawatar mawa bata sake sha’awar shan wani abu ba dan sun gagareta. Hasalima data tuna sai zuciyarta tahau tashi kamar wadda ta tuno wani abinci. Wannan dalilin ne ya zare mata duk wani tunanin ɗaukar wani abu tasha ya bugar da ita. Sosai wannan zuwa na su Tajuddeen da jin zaiyi zaman aiki anan yasata shiga dogon tunani, bata sha’awar tunkarar Nigeria sam, dan harga ALLAH wani sashe na zuciyarta na tsoron haɗuwa da Uncle Yousuf, sannan kuma bazata iya cigaba da zama a ƙarƙashin inuwa ɗaya da Tajuddeen ba. Dolene tasan mafita na barin ƙasar zuwa wata ƙasa daban ta karasa dogon hutun data ɗauro ɗammarar yi har sai sanda taso ta waiwayi gida Nigeria sannan. Kasancewar anan ba wani an damu da dare ko rana bane dan akoda yaushe ba fasa sabgoginsu suke ba sai in sanyin gari ya hana hakan yasa Lulu tunanin ɗan fita yau tasha iska. Miƙewa tai duk da yanayi rashin ƙarfin jikin da take ji ta sake sabon shiri cikin wando da riga da jibgegiyar rigar sanyi mai hula. Turare taɗan ƙarama jikinta ta ɗauki ƙaramin ledan chocolate ɗinta ta saka a aljihun rigar bayan ta ɗaure igiyar takalmanta ta fito. Tajuddeen kawai ta samu zaune a falo yana daƙilar waya. Kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta. Shiko da sai da taɗan gittashi ƙamshinta ya dakar masa hanci ya sashi farga da ita da sauri ya ɗago. Ganinta da shirin fita ya sashi miƙewa da sauri yana faɗin, “Ƴammatan ina zuwa haka ba neman abokin rakkiya?”.
“Ba buƙata”.
Ta faɗa a daƙile tana ficewarta, kafin ya iso ƙofar ta maida ta rufe da sanya security ta baya tana hararar ƙofar da jan tsaki tai wucewarta. Sororo Tajuddeen ya tsaya bayan ya gama mummurɗa handle ɗin ƙofar ya tabbatar da ta kulle ta baya. Lips ɗinsa ya ciza da yanayin rashin jin daɗi ya koma ya zauna a inda ya taso. Itako Lulu cikin tura hannayenta dake sanye da Safa suma a aljihun rigarta ta fara tafiya bisa lafiyayyen titin street ɗin nasu a hankali dusar ƙanƙara na ɗan sauka mata a jiki ɗis-ɗis kaɗan-kaɗan. Duk da akwai sanyi sosai yanayin ya mata daɗi, dan rabonta da irin wannan fitar haka tun bayan gama jiyyar jikinta da Smart ya murza, tana kuma ɗan fara samun walwalar ta kwana biyu sabon yanayin ciwon nan ya sake kwantar da ita shima. Tayi nisa sosai da gidan ta samu wani shagon shan coffee ta shiga, coffee ɗin tasa aka kawo mata, sai dai tana kaisa bakinta taji zuciyarta ya fara tashi, a take ƴan cikinta suka shiga hautsinawa. Babu shiri ta baro gurin cikin tashin hankali bayan ta biyasu, duk yanda taso riƙe aman ya gagara dole ta koma cikin restroom nasu ta dinga sheƙasa har ɗan kunun gyaɗar da tasha a gida sai da ta zazzagar. Cikin galabaita ta samu ta wanke fuskarta ta fito dajan ƙafa. Can gefe ta samu ta sake zama tana maida numfashi ɗaɗɗaya zuciyarta a cunkushe da tunanin wai mike damunta haka ne?. Ita dai tunda take bata taɓa fuskantar kalar ciwo haka ba da amai. (Ni dai nace Hummm). Ta jima a shagon coffee ɗin kafin ta miƙe cikin ƙarfin hali ta sake nufo hanyar dawowa gida dan wani irin sanyi mai shiga jiki da ƙashi take jin na ratsata duk da yanda ta rufe duk jikinta da kariya harda su Safar hannu da facemask amma bata tsira ba. Da ƙyar ta iya kawo kanta gida, ta cire security ɗin data sakama ƙofar saboda Tajuddeen ta shigo cikin tangaɗi. Babu kowa a falon da alama Tajuddeen ya shige, gudun karma wani yazo ya sake damunta ya sata nufar bedroom ɗinta dan yau tayima Dada yaji akan bazata sake kwana a ɗakinta ba. Dan dama da nata zuwan Dadar ya sata komawa inda ta sauka kasancewar bata da lafiya. Gaba ɗaya hankalin Dada da Alh. Sulaiman da suka haɗe kansu a bedroom ɗin Lulun da tunanin bazata shigo nan ba koda ta dawo yanzu baya kan ƙofar, tattaunawa suke game da zancen cikin da suka saka aka zubar mata batare da tasan ma da cikin ba. Wani irin bugawa ƙirjin Lulu yay da ƙarfin gaske. Ta tsaya cak tamkar wadda aka dasa matsayin gunkin tarihi ba mutum mai numfashi ba tana cigaba da saurarensu. Kanta ne ya fara juyawa sannu-sannu ta fara ganin hajijiya babu zato sai jin faɗuwar abu sukai ƙasa yifff. A tare suka zaburo tare da kallon ƙofar cikin waro idanu…..
Bayan kamar awanni biyu ta dawo a hayyacinta, zuwa lokacin hatta da Tajuddeen na a ɗakin zaune a gefenta cikin damuwa dan har fuskarsa ta gagara ɓoyewa. Ɗaya bayan ɗaya ta gama binsu da kallo tamkar mai son tantancesu kafin ta maida idanun nata ta lumshe kawai batare data nuna alamar ta tashin ba. Hirar kakar tata da kawun nata ne suka shiga dawo mata dalla-dalla, ita Mawaddat ce keda ciki, ciki na haihuwar ɗan mutum, amma suka saka aka zubar da shi. To minene dalilinsu nayin hakan. Duk da a karan kanta bazatace son cikin take ko akasinsa ba, amma tanaji a ranta kamar ya kamata ace kafin su aikata zubar da shi a bari ta sani da kuma jin ta bakinta ai. Hannunta dake ajiye a saman cikin nata ta motsa a hankali, tare da sake matsar da shi ƙasa sosai ta shafa cikin. Wannan ne ya fargar da su Dada cewar ta farka. Gaba ɗayansu sukai kanta da sannu musamman Tajuddeen da Dada. Dan Alh. Sulaiman dai idanu kawai ya zuba mata batare da yace komai ba. Cikin damuwa Tajuddeen ke jera mata tambayar mike damunta? Ko zata tashi suje asibiti ne? Yanzu ina ke mata ciwo?. Idanun nata ta ɗan sake buɗewa ta kallesa, sai kuma ta maida abinta ta lumshe. Sake jera mata sannu da roƙon ta bari ya kaita asibitin yayi. Amma sai ta girgiza masa kanta kawai. Zai sake magana Alh. Sulaiman ya katseshi da faɗin, “Tajuddeen relax mana”. Shiru yay badan yaso ba, hakan yasa ɗakin komawa shiru. Lulu da gaba ɗaya take jin wani irin yanayi mai kama da jin zafi da ɗaci a zuciya ta sake buɗe idanunta da sukai ja akan Dada. Muryarta irin ta mara lafiya a dake ta ce, “Dada nice na samu ciki aka zubar?”. Ba Dada ba hatta Alh. Sulaiman sai da furucin nata ya razanashi. Kusan a tare suka kalli Tajuddeen da ya furta “Ciki kuma Mawaddat?!”. Maimakon amsa Tajuddeen ɗin Dada take kallo alamar jiran amsa daga gareta. Dada data ɗan daburce cikin inda-inda ta ce, “E… E… Eh hakanne Sweet heart. Mun…m…munji tausayinki ne da ganin halin da kike a ciki na wahalar ciwo. Sannan minene amfanin haihuwa da wancan sankaran shashashan yaron da ko kansa bai iya riƙewa ba sai baƙin talauci, ke akaran kanki ma baki isa haihuwar ba ai shekarunki nawa ma duka. Na biyu inaji a jikina bada yardarki aka samu cikin nan ba, sai dai in asiri yay miki tare da fyaɗe. Dan ke da bakinki kin tabbatar min baki taɓa bashi kan ki ba. Ki faɗa mana gaskiya, fyaɗe yayi miki ko?”.
Kai Lulu ta kauda tana mai lumshe idanunta batare data bama Dada amsa ba, dan wani irin zafinsu takeji kamar ta shaƙo ɗaya a cikinsu ta maƙure kawai, a mamakinsu sai ganin hawaye sukai na zirara ta gefen idonta yana sauka saman filon da take kai har a cikin kunnenta. Gaba ɗayansu babu wanda bai kasance a yanayin zama turus ba, musamman Tajuddeen da ke jin jikinsa na tsuma. So yake kawai yaji Lulu tace fyaɗe Smart yay mata, shiko ya ɗauki alwashin koda uwarsa yake yawo sai ya yagalgala masa rayuwa. Amma abin mamaki sai gashi iya lallaɓa Dada taima Lulu dan tace wani abu game da samuwar ciki taƙi tace komai. Da tagama zasu dameta sai taja bargo har saman kanta ta rufe kawai da faɗin “Not your business! Please live me alone”.
Wannan abin da tai ya ƙara sakasu a wasi-wasi, amma sai Alh. Sulaiman yace su manta da batunta tunda dai an ɗauki mataki, yanzu kawai abinda zasu maida hankali shine binciko inda Smart yake ya saketa a ɗaura aurenta da Tajuddeen. Sun gamsu da hakan, sai dai daga ƙarshe Dada ta bada shawaran in har fa anƙi ganin Smart dole ne su nufi Nigeria su makashi a kotu ta bama Lulu takardar saki kawai ko su nemoshi su dole ga amsa kiran kotu yazo ya bada ai. Nan ɗin ma sun gamsu, dan haka suka tsaya a bisa shawaran nan guda biyu…
Tun daga wannan magana Lulu ta koma musu shiru-shiru a gidan, dama ga yanayin rashin jin daɗin jiki da take fama da shi, wanda zuwa yanzu take kallon hakan a matsayin zubar mata da cikin da akayi ne. Su kuma su Dada ke fassarawa da asiri Smart yay mata kawai. Duk yanda Tajuddeen ke son shigema Lulu taƙi bashi fuskar hakan. Dole ya koma baya-baya da ita amma hakan na damunsa. Bama shi ba hatta su Dadan ta tattara ta watsar kamar bata san da su a gidan ba. Ummita kawai take kulawa dan yarinyar nada hankali da nutsuwa. (Ummita ta taɓa aure harda yara biyu, sannan zata iya girman Lulu kaɗan, wahalar da tasha wajen mijinta yasa bayan ya saketa iyayenta sukace bazata zauna musu a gidaba ta tafi wajen ƙanwar mamanta a Abuja. Karatu ta koma, bayan ta kammala rashin samun madogarar aiki ya sata amsar wannan aikin zuwa Canada ta hanyar Hajiyan Shuwa maƙwafciyar ƙanwar mamanta).
Duk da abinda Lulu ke musu duk abinda tace tana so sai Tajuddeen ya fita neman mata shi a cikin garin koda yana tunanin bazai samu ba. Duk da dai ma babu abinda tafi nacemawa a yanzu kamar kunun gyaɗa da fruits. Ita kanta har mamakin kanta take akan shan kunun gyaɗar nan na ƙaddara daya sarfaceta. Dan ita a baya ba gwanar shansa bace ba, zama ta iya rantsewa a ɗan zaman datai gidan Aliyu ne ta koya shansa. Sunan Smart da yazo mata a zuciya ya sata jan ƙaramin tsaki. Ɓal-ɓal taji cikinta ya bada har sai da takai hannu samansa ta dafa. Sai kuma akai shiru. Bata kawo komai a ranta ba ta watsar da batun Smart gefe da kan faɗo mata a rai musamman idan tayi wani abu haka daya tuno mata da zaman nasu. Sannu a hankali jikinta kuma sai ya fara sauƙi, zuwa lokacin Alh. Sulaiman da Tajuddeen sun wuce wai duba Baba Garko, sai dai a baɗini shi Alh. Sulaiman nashi zuwan akwai manufa. Ganin Lulu ta samu sauƙi ta murmure sosai sai ma wata ƴar ƙiba da murjewar jiki da ta fara. Dan tayi wani irin ƙyau na farat ɗaya da haske tare da ƴar ƙiba. Zuwa yanzu babu abinda ke damunta sai ɗan zazzaɓin dare. Da zaran ance sha biyu tayi zazzaɓi zai rufeta, zuwa gabannin asubahi kuma sai ya sauka ta wayi gari garas tamkar komai bai faru ba. Shan kunun gyaɗa kam sai abinda yay gaba. Tana nan tana abunta. Tun Dada na maganar wannn shan kunun gyaɗa data laƙama suna na fitina har ma ta kawo ido ta zubama Lulun kawai………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 7️⃣
……..Kwanan Dada goma sha ɗaya ta fara shirin komawa wajen mijinta. Lulu ko ta maƙale tace ƙafarta ƙafarta dan bazata sake zama ita kaɗai anan Canada ba ciwo ya halakata. Cikin lallashi Dada ta nuna mata bazai yiwu ba, ta kwantar da hankalinta ai Tajuddeen na dawowa nan ɗin duk da ba’a gidan zai zauna ba. Tsaf ta tubure cewar ai ita ko ƙasa ɗaya ma bazata zauna da shi ba. Tunfa Dada na lallashinta harta birkice mata da masifa cikin ɓacin rai. Amma hakan baisa Lulu ta yarda zata cigaba da zama a Canada ba. Sai ma cewa tai ita gida Nigeria zata koma to. Tofa babbar magana, hankalin Dada ya tashi, dan tasan taurin kai irin na Lulu sarai. Alh. Sulaiman tai kira ta sanar masa. Washe gari sai gashi ya sake dawowa Canadan. Shima balbale Lulu yay da bala’i tare da zageta tas ita da Daddy sannan ya saka Dada tattaro masa passport ɗin Lulun da komai da zai iya taimaka mata fita a ƙasar ya wuce da su harda na Ummita ma. Wannan abu ya tada hankalin Lulu, hakama Dada sai al’amarin ɗan nata ya fara bata mamaki kuma. Dan sai take ganin ya zafafa da yawa, miye na ɗauke passport kamar wasu masu son kidnapping yarinya?. Amma ta kasa iya masa magana dan harga ALLAH tana shakkar ɗan nata kasancewarsa ba kanwar lasa bane ba.
*_NIGERIA_*
Alh. Sulaiman ya koma Nigeria bisa matsawar Tajuddeen dole yakai kotu akan alƙali ya saki Lulu, amma sai ya bashi amsa da cewar sai ma’aurata duka sun gurfana a gabansa zai iya aikata hakan. Zancen ya matuƙar bashi haushi ya yayyaɓama alƙalin magana duk da kuwa suna mutunci. Shiko yay biris da shi dan yace bazai aikata abinda ya saɓaba, taya zai kama kashe aure ma babu masu alaƙa da auren kamar a garin da babu shari’a, to yace yamawa hukunci kenan. Kusan alƙalai biyu ya sake tunkara bayan na farko amma amsar duk iri ɗaya ce suma since sai ma’auratan sunzo, dan koda aka aika sammaci gidan su Smart sai akace ma nai kai takardar ai Smart bama ya ƙasar, bakuma asan randa zai dawo ba ma. Alƙalin ƙarshe ne ya bukaci ganin iyayen Smart. Koda Abba yaje sai ya nunama Alh. Sulaiman yafisa sanin takan duniya, dan cayayma alƙali ai yaron da matarsa suna tare acan turai, shi Alh. Sulaiman shirmensa kawai yake yi, yasa a kira masa Smart a waya, akayi kuwa sa’ar samunsa, sun tattauna sosai da alƙalin akayi sa’a kuma shima Smart ɗin yace yana tare da matarsa Alh. Sulaiman yana shirmensa ne kawai saboda yana son raba auren dan taƙi ɗansa. Alƙali kuwa ya samu Alh. Sulaiman yay masa tas tare da gagaɗin yabar wannan shirmen da zubda mutunci yara su rayu da juna tunda sunce suna tare, ɗanshi kuma yaje ya nema wata. Wannan makirci ya matuƙar ƙona masa zuciya, dan haka ya ƙullaci Abba a ransa da fara shiri na musamman….
Taƙaddamar Daddy da Alh. Sulaiman ta matuƙar sake ɗaukar zafi a wani yanayi shi da abokan haɗin kansa su Hon. Nakowa. Duk da dai Alh. Sulaiman ɗin bawai ya fito ya faɗa musu komai da komai bane a tsakaninsa da Daddy bayan wanda ya shafesu su duka ba, dan shi yana nuna musu TAKUN SAƘARSA da Daddyn dai iya tasu ce data shafesu. Bai kawo ɓoyayyen al’amarin dake a tsakanin su sam. Sun ƙara shirya sabon plan akan Daddy, tare da shiga kogin tunani da binciken ta yanda yake bibiyar al’amarin su. Musamman ma shi Alh. Sulaiman da yaji har poisoning ɗin mahaifinsa da yasa akayi wai Daddy ya sani. Wannan zance ya matuƙar tada masa hankali, dan daga ALLAH sai shi sai yaronsa Malami suka san wannan sirrin. Duk da dama gubar da suka bashin bata kisa bace, wadda zata kwantar da shi jiyyace kawai na tsawon watanni harya samu kammala shigo da abubuwansa wanda ya tabbatar da in har mahaifin nashi na tsaye akan ƙafafunsa za’a iya samun matsala a wannan karon. To Alhmdllh burin nasa ya cika, dan kayayyakinsa da suka taso daga ƙasar Mexico sun iso lafiya, inda cikin nasara yay hada-hadar rabawa customers ɗinsa shi da abokan Business ɗinsa da ayanzu sukafi ƙarfi a kudancin Nigeria. Bawai baya huɗa da hausawa ƴan arewa bane akan harkar, akwai su jefi-jefi a cikinsu, sai dai sunada tsoro matuƙa ba kamar ƴan kudancin ba, sunfi yarda su zama dilolin cikin gida bawai masu ɗakkowa daga wajen ƙasar ba. Sannan wasun su basa fito musu da kurwarsu a fili sai dai kawai ace business ne na kaya ko wani abu idan an haɗa sai a sakko kayan da suke shigowar da shi. Akan samu matsala idan mutum ya farga da wuri, dan mafi yawan hausawan da ake riftawa a ciki da zaran sun gane sukan zare hannunsu, sai ƙalilanne da ga ciki masu busashiyar zuciya da son dukiya ke afkawa a cigaba da harka kawai. Wasu kuma tsoro, dan daya zamana ka gane ka fidda kanka to lallai sai su Alh. Sulaiman sun kashe ka ta inda babu wanda zai gane su suka aikata. Hakan shine ya faru Da Daddy, dan kuwa dai Alh. Sulaiman yaja Daddy a jikinsa lokacin daya fahimci shine babban yaron mahaifinsu na gaban goshinsu da yake tsindum akan harkar shigar kuɗi da fitarsu, saboda duk wani babban business na ƙasashen ƙetare na Alhaji Sufi Garko Daddy shine tsaye akai. A lokacin Alh. Sulaiman yana buƙatar kuɗi masu yawa domin shigo da kayansa, sai dai kuma yana tsoron tunkarar mahaifinsa da batun dan bazai bashi ba kai tsaye sai ya bisa da tambayar ƙwanƙwanto. A hankali yayta hillatar Daddy da sunan abota har suka zama aminai ma sosai, kamar wasa ma sai shaƙuwa ta gaske ta fara shiga tsakaninsu ba kamar yanda Alh. Sulaiman ɗin ya tsara ba da farko. Tafiya tai zurfi sosai tsakaninsu har Alh. Sulaiman ya fara jan ra’ayin Daddy suka ƙulla alaƙar business na kawo motoci, sai dai kafin hakan sai da ya fara kafa masa tarko na musamman akan dukiyar mahaifin nasa, inda wasu manyan kuɗi suka dulmiye Daddy ya rasa yanda akayi, hankalinsa ya tashi matuƙa a lokacin, amma sai Alh. Sulaiman ya kwantar masa da hankali tare da maye gurbin kuɗaɗen da aka rasa ɗin yace Daddy ya dinga biyansa a hankali, wannan yasa Daddy sake sakin jikinsa da shi saboda rufa masa asirin da yake gani yayi akan abinda bai taɓa faruwa ba dan shi mutum ne mai takatsantsan da gaskiya shiyyasa Alhaji Garko ya yarda da shi matuƙa, shi kuma tsoron rasa wannan yardar daga mutumin kirki irin Baba Garkon ya sashi shiga a tashin hankali lokacin da kuɗin suka salwanta, iya bincike kuma bai iya gane komai ba. Sun fara business na safarar motoci daga waje zuwa gida Nigeria. Wannan shine silar buɗe *_JIƘAMSHI MOTO’S_* Kamar abin arziƙi Business ya fara tafiya yanda ya kamata, alhkairai suka ƙara buɗe hanyar shigoma Daddy tako ina. Cikin ƙanƙanin lokaci ya sake ɗagawa dukiya ta sake zama a hannunsa ya kuma biya Alh. Sulaiman kuɗinsa. Hakan ya saka Alhaji Garko a farin ciki, dan shi irin mutanen nan ne marasa baƙin ciki wana ƙasa da su. Maƙudan kuɗi ya sake bama Daddy akan ya ƙara a business ɗin, duk da kuwa dama can bawai ya barsa haka bane ba, yana masa alkairin tare da fidda masa hakkinsa na albashi mai tsoka. Amma sai wannan karon ya kasance na musamman, ba komai yaja ra’ayinsa dayin haka ba kuwa sai ganin yanda Daddy shima ya fara sanin ciwon kansa. Alh. Sulaiman da Daddy da sabbin abokan daya sani a dalilin Daddy su Alh. Misau sun cigaba da juya taro yana komawa sisi batare da Daddy yasan ainahin sirrin kasuwancin nasu ba bayan abinda aka sanar masa, dan ta ƴan bariki kawai ake masa da sunan shigo da motoci da babura, da wasu nau’o’in kayayyakin daban-daban. Sai da shekaru suka ka kusan huɗu a tsakani sannan ya farga a dalilin wani lokaci yaga cocaine da ga cikin kayan nasu da aka killace a store batare da su Alh. Sulaiman sun san yaya akai basu cireta ba sanda suke cire sauran. Hankalin Daddy yay masifar tashi a wannan ranar, dan ya horu da ƙyamatar harkar shaye-shaye ma gaba ɗayanta a dalilin yanda ubangidansa Alhaji Sufi Ado Garko ya tsanesa matuƙar tsanar da sai da ya shiga ya fita da dukiyarsa cikin gwamnati aka kafa babbar hukuma da in ta kamaka da irin wannan kayan sunanka sorry kawai. Daddy baida yawan faɗa sam, sai dai mutum ne mai zuciya idan ka kaisa maƙura. Dan haka a wannan ranar ma ya tunkari Alh. Sulaiman cikin tashin hankali. Shima Alh. Sulaiman ɗin ya girgiza matuƙa shi da abokan huɗɗarsa, saboda suna kiyaye duk wani abinda zai iya kai idon Daddyn, amma sai gashi aiki ya buɗe a gaɓar da suke cin moriyar al’amarin fiye da baya. Da gaggawa sukai zaman meeting na musamman akan dolene fa a kawar da Daddy a duniya kamar yanda akema duk wanda ya nema bijirewa. Sai dai mi Alh. Sulaiman yay saurin ƙwaɓarsu akan karma su fara wannan taɓargazar, dan duk wani motsin Daddy a idon mahaifinsa Alhaji Sufi Garko yake, saboda yanda yake ƙaunarsa. Ya tabbatar musu idan suka taɓa Isma’il Jiƙamshi cikin ƙanƙanin lokaci komai zai buɗe musu, sudai jinkirta suyi tunani. Wannan furuci na Alh. Sulaiman shine ya kawo rabuwar kai, dan wasu na ganin ai yayi hakanne saboda Daddy abokinsa ne kawai, sannan yaron mahaifinsa. Amma inba hakaba su sauran da suka kawar ai akwai na jikinsu suma. Duk yanda Alh. Sulaiman yaso su fahimceshi hakan bata faru ba akai baran-baran. Wannan shine dalilin rabuwar Alh. Sulaiman da su Hon. Nakowa. Sannan yay amfani da wannan damar ya nunama Daddy goyon baya tare da tsarashi kan cewar shima bai san komai ba yaudararsa akeyi kamar yanda shima Daddyn akai masa, amma ya fita da ga wannan gaɓar. Hakan ya bama Daddy nutsuwa, inda ya yarda da Alh. Sulaiman ɗari bisa ɗari suka cigaba da amintakarsu tare da cigaba da business ɗin motocinsu kamar yanda suka fara. Sai dai fa a yanzu Daddy a ankare yake ƙwarai da gaske. Wannan ya saka Alh. Sulaiman canja taku. Shekara biyu da faruwar haka Mawaddat mahaifiyar Lulu ta dawo Nigeria daga karatu. Akwai shaƙuwa matuƙa tsakanin Mawaddat da Alh. Sulaiman yayanta, dan suna ɗasawa matuƙa duk da dai ita kowa a gidansu na sonta da ji da ita kasancewar itace mace sai autarsu, sai ƴaƴan ƴan uwa da Dada ta riƙa mata. Ƴar cikinsu dai su biyun ne kawai mata ita da auta Sultana. Akwana a tashi da dawowar Mawaddat Nigeria ALLAH bai haɗata da Isma’il Jiƙamshi da take yawan ji a bakin mahaifinta da ƴaƴanta ba sai a randa yazo gidansu game da kawo takardun matarsa da Alhaji Sufi yace a kawo. Wannan kuma shine karo na farko da ya shiga gidan shima dan duk iyakar huɗaɗarsu da Alhaji Garko da Alh. Sulaiman iyakarsu office ne da ma’aikatu, sai kuma gidan Alh. Sulaiman ɗin wannan Daddy yasha zuwa. So ne farat ɗaya ya shiga zuciyar Lulu, sai dai ta fahimci bazata taɓa samun kulawar wannan haɗaɗɗen guy ɗin ba (Sannan su Daddy anaji da ƙarfin samartaka ba’a ruɓe ba😂🙏). Ta nema shawaran Yayanta Sulaiman dan babu wani kunya ko shakku ta sanar masa. A lokacin dariya Alh. Sulaiman ɗin yayi da faɗin, “Anya kuwa zaki iya Kandala? Dan yanada mata da yara biyu twins sannan shi ba ɗan kowa bane face wanda Baba ya ɗaga darajarsa ta hanyar ɗaurasa akan dukiyarsa”. (Dan sukan kirata da sunan Kande ne saboda bayan haihuwarta ita ɗaya tilo a cikinsu mace Dada ta sake jimawa bata haifi mace ba sai a haihuwarta ta ƙarshe ta haifi autarsu mace mai suna Sultana, sai dai Sultana sikila ce ko isashen lafiya bata da shi yarinyar. Gata da wayon tsiya da shiga rai)………✍️
_Ayi haƙuri mu cigaba a next page muji sauran._
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣
……..Farrr Mawaddat tai idonta a lokacin irin na wayayyun mata shagwaɓaɓɓu kuma ta ce, “Yaya mizai hanani iyawa. Matarsa bata gabana dan na ita zan auraba ai, kasancewarsa ba ɗan kowa ba, yawan ƴaƴansa duk baya gabana shi dai ɗin nake so ni dai. Idan kuma ban sameshi ba zaku iya rasani. ” cikin sauri Alh. Sulaiman yace, “A’a rufa mana asiri Kandala, indai Isma’il ne ki ɗauka kin samesa an gama”. Taji farin ciki da jin furucin yayan nata ƙwarai da gaske, dan tasan zai mata ɗin kamar yanda ya faɗa. Sai dai mi koda Alh. Sulaiman ya tunkari Daddy da batun sai ya nuna shi sam baya ra’ayin ƙara aure, matarsa ƴar uwarsa uwar ƴaƴansa ta wadatar da shi”. Ran Sulaiman ya ɓaci, amma sai ya danne kawai. Bai so Mawaddat taji wannan al’amari ba sai dai tama riga taji su da kunnenta, wannan yasa ta tada hankalinta matuƙa. Tare da tunkarar mahaifinsu a wannan karon kai tsaye. Shi Alhaji Garko harga ALLAH yayi farin ciki, dan Isma’il Jiƙamshi yarone haziƙi mai hankali da tarin nutsuwar da kowane uba zai so haɗa zuci’a da shi, amma bazai masa dole ba zai dai masa irin na manya. Dan haka ya sallami Mawaddat akan cewar ta jirashi zaiyi magana da Daddy. Mawaddat tayi farin ciki, dan haka ta koma gefe sauraren mahaifinta, sai ma nemar aiki da tayi a inda Daddy yake dan kawai ta dinga ganinsa a kusa da ita. Alhaji Garko bai samu damar yin magana da Daddy ba har tsawon watanni kusan biyu saboda busy da yay da ga shi har Daddy ɗin. Mawaddat taso sake tunkarar mahaifinta da batun sai dai bata samu zama da shi ba saboda yay busy da yawa ƙasar ma ba sama yake ba. Amma tanata fakonshi. Ranar wata Lahadi data shiga a tarihin da Garko family bazasu taɓa mantawa da ita ba ta riskesu a ƙarshen wannan sati da ake saka ran dawowar Alhaji Garko daga dogon fatauci da ya tafi. Wato autar wannan zuri’a da kowa ke ma gata da tattali da ƙauna da tausayin halin da take a ciki mai kimanin shekaru tara a duniya Sultana aka wayi gari wani azzalumi yay mata fyaɗe, sai gawarta aka tsinta a can farkon layi ƙasan wata bishiyar dalbejiya na ƙofar wani gida. Wannan al’amari ya girgiza wannan gida tare da mamaki matuƙa akan tayaya Sultanar ta fita daga gida har hakan ta faru?. Dada dai tasan ta tafi islamiyya da ake kaita a mota a ɗakkota, ta kuma tabbatar da ta dawo gab da magrib, daga nan bata sake ganinta ba a tunaninta ta kwanta ne a ɗaki, dan yanayin jikinta na masu sikila yasa bata da kwaramniya sam. Sai da kusan sha biyu taje leƙata sai ta samu ɗaki wayam. Da farko bata damuba ta shiga kwala kiran masu aikinta da tambayar Sultana. Sai dai amsar ɗaya ce su basu sani ba, dan tunda ta dawo islamiyya basu sake ganinta ba. Cikin ƙanƙanin lokaci Dada ta birkita lissafin kowa na gidan, dan gaskiya ALLAH ya jarabcesu da ƙaunar Sultana matuƙa, kodan tazo a ƙarshe ne batare da tunanin zuwan nata ba. Iya bincike babu Sultana a cikin gidan, dan haka nema ya koma har waje bisa zargin ko sanda ake sallar magrib ta silale ta fita duk da kowa yasan hakan ba halin yarinyar bane. Cikin amincin ALLAH kuwa sai ga ta an ganta, sai dai cikin jini kuma babu rai. Hakan bai hana a garzaya da ita asibiti ba, inda a gwaje-gwajen farko doctor ya tabbatar musu fyaɗe akai mata, amma ta farfaɗo daga doguwar sumar data tafi. Hankalinsu ya tashi, sai dai jin tana raye yasa sun ɗan ji sassauci. Alh. Sulaiman ne ya kawo police aka tattare duk ma’aikatan gidan zuwa police station. Harda kukansa kamar wani ƙaramin yaro, bayan lokacin har Auta an haifa masa Tajuddeen. Bin cike iya bincike ba’a gane komai ba, inda Sultana da ake tunani da murnar ta fara samun lafiya a wani dare tabar duniya. Dan haka kawai aka samu tana fisge-fisge da girgiza irin na firgitar wanda ya tsorata, duk da tana yin hakan dama tunda abin ya faru sai na ranar yafi na kullum. Da ƙyar doctor suka iya kwatanta ceto numfashinta, da ga ƙarshe dai tace ga garinku nan. Mutuwar Sultana ta zama kamar wata mutuwar babba a gidan, dan kowa ya koɗe ya jeme saboda kuka, sai dai halin da Mawaddat ta shiga yafi na kowa a gidan. Har asibiti ta kwanta na tsawon kwanaki kafin ta dawo dai-dai. Watanni sun ɗan sake shuɗawa har zukata suka haƙura da shiga dangana game da Sultana, yayinda jami’an tsaro ke cigaba da bincike, sai dai maimakon a cikin gidan sai hankalinsu ya fara karkata waje akan cewar ƴan hamayyane kawai sukai hakan. A ranar da Sultana ke cika wata biyu a cikin ƙasa Mawaddat ta tunkari Daddy da al’amari mai firgitarwa game da abinda ya faru da Sultana, inda ta nuna masa video data ɗauka a lokacin suna a cikin ɗaki tare da Alh. Sulaiman ga Sultana yashe cikin jini. Tare da ɗakko masa zancen da ya san bayan Alh. Sulaiman da shi sai UBANGIJI kawai suka sani, wato ɓatar maƙudan kuɗaɗe a hannunsa wanda yayanta Alh. Sulaiman ɗin ya ranta masa ya biya batare da sanin mahaifinsu ba har yanzu. Iya ƙoƙarin yayi danta fahimci gaskiyar al’amurin amma ta nuna sam bata da wannan lokacin, sai ma barazana data fara masa na in har bai aureta ba to lallai zata fallasa wannan video a gidansu dan kowa yasan yanda akai suka rasa Sultana. Hankalin Daddy ya tashi matuƙa, sai dai Mawaddat ta masa mugun ƙullin da yay imani da in har bai aikata yanda take so ba tofa lallai bashi da wata mafita. Dole badan yaso ba ya amsa mata, tare da tunkarar mahaifinsu Alhaji Garko da batun yana son aure Mawaddat. Alhaji Garko yayi farin ciki, yayinda Dada tai tsalle ta dire tace sam bata yarda ba. Ankai ruwa rana sosai game da wannan aure, dan an samu rabuwar kai wasu na goyon bayan Dada, wasu Alhaji Garko da Mawaddat. Inda dai daga ƙarshe bayan an cuɗa an cuɗo ALLAH yay wannan aure da babu wanda yasan manufarsa sai ALLAH sai kuma su ma’auratan. Mawaddat ta shiga gidan Daddy da gigiwar izza da gadara, inda daya motsa zai taka mata birki tamai barazana da wannan video recording da maganar kuɗaɗe. Hankalinsa a tashe yake, yayinda Mommy da Uncle Yousuf suka kasa fahimtar halin da yake a ciki lokacin duk da yanda yake son fahimtar da Mommy amma sai kishi ya rufe mata ido ta kasa fahimtar ba dukiya ko wani matsayi bane ya sashi aikata yin auren ma kansa balle biyema iskancin Mawaddat a gidan. (Wannan shine kuskuren Mommy. Mata ya kamata mu dinga sanin kowanne yanayi da mazajenmu suka shiga koda akan mace ne. Mu dinga sassauta kishi a wasu gaɓoɓin rayuwa dan wani abun kanzoma bawa ba yanda ake kallonsa ba.) Daddy yata gwada son sace camara ɗin nan daga wajen Mawaddat sai dai a ankare take da duk wani motsinsa. A magana ta gaskiya a zamanshi da Mawaddat bai taɓa jin sonta ba kona yini ɗaya, dan ko’a harkar auratayya ita ke kiɗanta ke rawarta game da shi. Sai dai yana yin dauriyar sauke hakkinta har ALLAH yasa aka samu cikin Lulu, sanadin cikinne ma yasa shi ɗan fara sassauta zuciyarsa. Hatta da son ƙyautatama Mommy idan yay niyyar yi Mawaddat kan masa barazana, ga shi Mommy taƙi fahimtarsa, a kullum kawai tana kallon yana cutar da rayuwarta saboda ya auri ƴar masu kuɗi ƴar ogarsa. Ana baifi sati guda a haifi Lulu ba a wani dare yana tsaka da barci Mawaddat ta tashesa. Hakan ba sabon abu bane da take masa, sai dai kuma bayan tashinsa cikin ɓacin rai ya fahimci tashin yau yasha banban da wanda take masa a baya. Dan a mamakinsa ma sai gata durƙushe gabansa a ƙasa tana hawaye da neman gafararsa akan duk abinda ta aikata masa. Ta ce, “Isma’il dan ALLAH ka yafe min, nasan na aikata abubuwa masu yawa a gareka tare da tilastaka aurena badan kaso hakan ba. Na kuma azabtar da matarka itama ta hanyoyi da dama. Ba komai ya jawo hakan ba sai ɗunbin so da ƙaunar da nake maka har ƙasan zuciyata. Duk da inajin kishin matarka banso shigowa cikinku ta wannan sigar ba. Sai dai komai ya canja a dalilin wannan video na fyaɗe da kukaima Sultana kai da Ɗan uwana Sulaiman da kuma kuɗin daka salwantar a Companyn mahaifina bisa son zuciya kamar yanda ma samu labari. A ranar da kukaima Sultana abun nan nayi kuka kamar zan mutu tare da jin tsanarku irin wanda ban taɓama wani mahaluki a duniya ba, na saƙa abubuwa daban-daban akan ku a ciki harda shafe numfashinku a bayan ƙasa. Sai dai zuciyata ta gargaɗeni da yin hakan tare da bani shawarar na dafaku da ranku cikin ruwan sanyi. Na fara da kai ne ta hanyar maka barazana harka aureni, tare da nisantaka da matarka da nasan kana matuƙar so da ƙauna. Da farko naso na haɗa harda Yousuf, sai dai nutsuwarsa da hankalinsa yasa naji tausayinsa nama tsaya masa akan ya tafi makaranta dan bana son yaga abinda na tanada muku. Burina sai na gama da kai sannan na koma kan rayuwar ɗan uwana Sulaiman shima, daga ƙarshe na fallasaku a idon duniya ku kunyata. Sai dai duk wannan lissafin nawa ƙaddara ta canjashi Isma’il a dalilin wannan cikin da ya shiga jikina a mistake, sau biyu ina yunƙurin zubar da shi amma hakan ya gagara, a karo na biyun ma sai likitoci suka tabbatar min idan na sake zan iya rasa kaina gaba ɗaya. Wannan yasa na haƙura na barshi badan naso ba. Sai dai kuma kana naka ALLAH na nashi, tashi kuma itace gaskiya. Wlhy Isma’il a ƴan kwanakin nan inajin kamar barin duniya ke gabatoni. Ji nake kamar bazan yi rayuwa mai tsaho ba. Shiyyasa na shirya faɗa maka gaskiya da neman afuwarka. Tare da baka shawarar kaima ya kamata ka fito ka sanarma iyayenmu gaskiyar al’amurin game da abinda kuka aikatama Sultana kai da Sulaiman koda bazaka faɗi maganar kuɗaɗe ba. Ku karɓi kowane irin hukunci hakan zaifi zama masalaha a gareku da zuri’arku gaba ɗaya”.
Sosai jikin Daddy ke rawa a wannan lokacin, ya kama kafaɗun Mawaddat ya tadata daga durƙushen da take ya rungumeta a jikinsa. Sai kawai ya samu kansa da sakin kuka. Itama saita shiga tayashi. Sosai sukai kukansu kafin su zauna dan bata jurar tsaiwa yanzu. Suna zaune a tsakkiyar gadon suna fuskantar juna hannunsa cikin nata ya ce,……..✍️
_🚴🚴🚴🚴Dan ALLAH wazai tayani typing._
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 9️⃣
………“Wlhy wlhy wlhy Mawaddat ban aikata komai ba wa Sultana, sannan ban san yanda akai muka rasa kuɗin nan ba a cikin Company, iya bincike kuma nayi amma ban gane komai ba har zuwa yau. Yanda kike kallon al’amarin ba haka yake ba. Kinƙi bani damar na warware miki ne tun farko shiyyasa amma yau zan sanar miki komai. Sai dai dan ALLAH ina son ki fahimceni, sannan kiyi bincike dan ki tabbatar da gaskiya ta. Ina zaune a gida tare da iyalina Sulaiman yay kirana hankali tashe yana kuka. Cikin sauri na shirya na nufi Garko house da yace min yana can a zatona ma wani abu ne ya faru da Baba wlhy, kasancewata ba baƙo ba a gidan yasa kai tsaye aka buɗen gate na shiga, hakan ya ƙara sakani sake shiga ruɗani, bayan nai parking nayi kiran Sulaiman ya sanar min na zagayo ta baya sashen masu aikin gidan yana acan. Na ɗan ji mamaki, amma sai bance komai ba nace masa ina zuwa. Wannan ne karo na farko danai ta wajen, da kwantace na shiga sashen dan alokacin duk masu aikin na can cikin gida suna aikinsu. Na samu Sulaiman zaune yana kuka ga yarinya gefensa kwance ya rufa mata bargo. A lokacin bansan matsayin Sultana a gidan ba, zamma iya cewa ranar ne nai mata ganin farko dan har sannan ba wani shiga gidan nake ba Sosai ai. Cikin tashin hankali da ruɗewar da nake a ciki nima na shiga jera masa tambayoyi. Da ƙyar ya iya sanar min fyaɗe yayma yarinyar. Kuma wlhy shi bada manufar hakan ba a zuciyarsa. Yazo ne wajen yarinyar mai aikinku dan sun saba kasancewa a tare kawai sai ya samu Sultana a ɗakin, kasancewar baya cikin hayyacinsa saboda abinda wai wani abokinsa ya yaudaresa ya basa da kayan maye a ciki kawai ya afka mata dan tana masa gizo ne like yarinyar da yake zuwa wajen nata sai daga baya ya fahimci abinda ya tafka ɗin. Kuka yake riris da roƙon na taimakesa, wlhy idan wani yasan wannan al’amarin to gaba ɗaya farin cikin family ɗin ku zai ruguje. Kai iyayenku ma zasu iya rasa ransu musamman ma Baba. Dan ya ɗauki son duniya ya aza akan Sultana kamar kowa na gidan gashi bata da isashiyar lafiya. Bani na aikata al’amarin ba amma wlhy na shiga matuƙar gigitaccen ruɗani a lokacin jin yarinyar ƙanwarku ce, dan wlhy bamma san sanda hawaye nima suka fara zubomin ba. Shine ya kawo shawaran yana son na taimaka masa mu kaita can waje ta yanda in mu ajiyeta kamar wani ne yay mata za’a fi saurin fahimta a kaita asibiti, muma kuma hakan zai fi bamu damar kaita asibiti da wuri karta rasa ranta. A ɗan gajeren tunanina a lokacin sai na fahimci hakan shine dai-dai saboda a ruɗe nake ni kaina bana iya gane komai dan tashin hankali, inba hakaba kafin a farga anan tabbas za’a iya rasata. Sannan su masu aikin zai zame musu tashin hankali. Ace a sashensu abun ya faru da ƴar masu gida dolene ace su nemo wanda ya aikata. Na biyu tashin hankalin daya tabbatar min Baba da Dada zasu iya shiga koma su rasa ransu. Wannan shine ya ƙarfafani muka ɗakko Sultana cikin duhun magriba muka saka a motata muka kawota ƙarƙashin bishiyar da aka ɗakkota. Bakuma mubar anguwar ba har sai da aka ɗauketa zuwa asibiti. Ban fahimci nayi kuskure babba a bama Sulaiman gudunmawa ba sai da na dawo gida nake bama Kareema labari kamar akan wani abun ya faru. Kalamanta ne sukai matuƙar rikitamin lissafi da zama nayi nazari nima. Matuƙar damuwa na shiga, har na yanke shawarar tunkarar Sulaiman da batun akan magana ta gaskiya mu fito kawai mu sanar da iyayensa gaskiya, musamman ganin yanda aka kama maigadinsu da wasu masu aikin gidan aka rufe kuma da taimakonsa ne koma nace shine ya saka akai hakan. Sai dai mi koda nai masa zancen sai ya shiga roƙona da kalaman da suka sake rikitamin lissafi, ina tsaka da neman mafita ke kuma kikazo da naki kalar salon..”
Kuka suka sake haɗe kai sunayi, sai da sukai mai isarsu sannan ta ɗakko masa camara ɗin ta bashi, hankalinsa ya tashi da ganin komai, dan tabbas duk wanda zai gani inba yasan gaskiya ba zai ce harda shi aka aikata, sai dai idan kai nazari a yanayin shi akwai sutura jikinsa saɓanin Sulaiman zaka iya fahimtar gaskiya. Laifinsa dai biyewa da yay aka fitar da Sultana a gidan. Roƙo sosai Mawaddat tai masa akan karya bar Sulaiman yasha ruwa a rayuwarsa akan wannan kuskuren har sai ya fito ya tonama kansa asiri, sannan maganar kuɗin Company ya binciki yayan nata sun salwanta ne da haɗin kansa, kuma kuɗin na hannunsa, dan taji suna tattaunawa da yaronsa Malami akan batun, sai dai ba komai taji ba da ƙyau gaba ɗaya. Wannan shine abinda take so ya mata koda bayan ranta. Ya tabbatar mata zaiyi amfani da shawaranta, dan yana son ya samu salama shima a ransa, hakan kuma bazata faru ba har sai ya fidda wannan ɓoyayyen sirrin da neman gafarar su Baba garko. Maganar kuɗi kuwa da tace ya bincika itama tai matuƙar girgiza masa zuciya, har ya fara shiga waswasi akan al’amura da dama game da abotarsa da Alh. Sulaiman ta rana tsaka. Kwana biyu da yin haka naƙuda ta tasarma Mawaddat, a lokacin daya samu Mommy na bata abu harga ALLAH a ruɗe yake, sannan ko Mawaddat ɗin ce tai mata haka a irin yanayin itama zai iya kawo hakan a ransa dan ya fahimci Mommy nada zafin kishi na masifa, shi da yake fuskantar ƙalubalen daga gareta shi yasan wannan saboda a zahiri da wahala ka gane tanada kishi a ƙanƙanin zama da ita. Dan ga wanda bai santa ba bazaice akwai ba, duk da yasan sun cuta mata, sannan tabbas tanada ƙyawawan halaye kishinne mai zafi kawai matsalarta, amma shi laifinta da yake gani shine kasa fahimtarsa da tayi tun farko. Lokacin daya ɗauki hanyar asibiti da Mawaddat cikin kuka dana azaba ta kamo hanunsa ɗaya ta ɗora a kan cikinta da faɗin, “Isma’il dan ALLAH ka yafe min, ka sake roƙamin matarka ta yafemin, ga amanar abinda ke cikina nan na baku, soyayya ta gaskiya daban samu daga gareka ba ina roƙonka dan ALLAH abinda zan haifa in har ya rayu shi ya samu. Kada ka bama kowa daga cikin ahalina abinda zan haifa ka riƙesa a wajenka ciki harda Dada. Idan da hali ma ka nisanta shi da su dan duk sanda Sulaiman yasan gaskiyar lamari kowane irin mataki zai iya ɗauka, kaima ka nisanta kanka daga al’amarin sa, inba hakaba wataran sai kayi dana sani, dan ƙarya yakeyi babu wani abokinsa daya bashi kayan maye da kansa yasha har cocaine yana sha dama, sannan ya jima yana lalata rayuwar masu aikin gidanmu, na taɓa tarar Dada da zancen amma bata yarda ba, sai ma balbaleni datai da faɗa akan idan taji batun a bakin wani saita ɓata min raina. Wannan dalilin yasa kaga na shige masa kamar munfi kowa shiri, amma ba haka bane ba, ina binciken abubuwa ne a kansa dan na jima ina zargin yana safarar miyagun kwayoyi a ƙasashe daban-daban musamman ƙasar Mexico, sannan yanabin hanyoyi daban-daban wajen ɗibar kuɗin baba. Na yi shirin idan na kammala bincikena na bama Baba bayanan ta hanyar gani da ido da zai tabbatar. Dan haka akwai abubuwa masu yawa da muhimmanci a cikin camara ɗin nan da suka shafesa sai kayi takatsantsan dan dama saboda shi na mallaketa…”
Wannan magana ta Mawaddat ta saka rayuwar Daddy sosai a wani hali bayan rasuwarta, shine dalilinsa na hana ahalinta jaririya daya maidama suna Mawaddat, tare da nuna mata soyayyar data roƙa garesa kuma yay mata alƙawari, wadda harga ALLAH bayan rasuwar tata kuma sai yake jin soyayya mai nauyi a kanta. Sai tausayin yarinyar da ya ringa ɗibarsa kuma shima. Dalilinsa na hana Mommy Mawaddat shawarar da yaji dangin mahaifiyarta na bata ne, hankalinsa ya tashi da jin abinda suka faɗa mata akan marainiyar ALLAH da batama san minene duniyar ba, sai dai ita Mommy bata san yaji ba. Yaso yay mata uziri amma jin itama ta karɓama ƴan uwan nata da cewar ai duk abinda Mawaddat tai mata saita ramashi akan Lulu ya saka zuciyarsa a razani lokacin. Dan baiyi tunanin kishin Mommy zaisa idonta rufewaba ta karɓi shawarar ƴan uwan nata. Wannan dalilan yasa ya sake tsayawa akan al’amarin Lulu ya hana kowa jingina da ita. Sai kuma ga abinda yafi na Mommy ya ɓullo masa, bai san yanda akayi Alh. Sulaiman yasan da camara ɗin hannunsa da Mawaddat ta bashi ba, kawai a wata rana ya samesa da batun a rikice, yace ya bashi camara ɗin Please. Amma sai shi Daddy kansa tsaye yace bazai bada ba har sai Alh. Sulaiman ya sanar masa gaskiyar al’amari game da harkar shigo da kayan shaye-shaye daya tsunduma shi, sannan ya faɗa masa gaskiya akan ya akai kuɗaɗen nan suka salwanta da kuma haikema Sultana a sashen masu aiki bayan kowa ya shaida bata zuwa can ɗin sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Wani banzan kallo Alh. Sulaiman yay masa tare da masa nuni da baida hankali. A kausashe ya ce, “Isma’il kai wanene da zaka titsiyeni? Yaushe ma ka kai inda kake tunanin ka kai ɗin? Kana almajirin gidanmu dan na jawoka kaci arziƙi har kake ganin idonka yay tsaurin sanin abinda ni kaɗai ya shafa. To daga yau ka kama kanka. Camara kuma idan baka bayar ta arziƙi ba zaka bada ta tsiya. Sannan ita wannan yarinyar ka shirya dan dolene na hukunta rayuwarta da laifin mahaifiyarta, dan ni bana yafiya bana kuma barin bashin gaba. Sannan sabo da kaza a wajena baya hanani yankata. Ba ita data zama ɗiyar ƙanwata ba, ko ita ƙanwar tawa da tana raye saina ɗan ɗana mata azabar sanin ainahin Sulaiman, amma duk da haka wannan ƴar tata zata fansheta ne”.
A lokacin tsawa Daddy ya daka masa, sai dai kafin yace komai Alh. Sulaiman ya bar wajen.
Wannan ne sanadin komai da zama mafarin ɗauke Lulu daga Nigeria Daddy ya maidata Garmany ya nema mata Nanny da tunanin ya kuɓutar da ita daga sharrin Alh. Sulaiman, shine kuma mafarin duk wani rikicin dake a tsakaninsu, dan har yanzu dai camara na a hannun Daddy duk barazanar da Alh. Sulaiman ke masa yaƙi bashi ita. Ya kuma kasa gayama kowa ciki harda Uncle Yousuf da Mommy dama Baba Garko….
Wannan kenan.
*_★CANADA★_*
Zuwa yanzu wata irin nutsuwa ce ke saukarma Lulu maiban mamaki, yayinda girman da cikinta keyi ya fara ɗaukar hankalinta. Da farko ta ɗauka tunbi ta fara tarawa, hankalinta ya tashi ta fara tunanin ko kunun gyaɗar da take shane ya kawo mata haka. Ta yanke hukuncin fara fita motsa jiki kawai da alƙawarin daina shan kumun gyaɗa duk da tasan hakan bamai yiwuwa bane. Sai dai bata san yaya zatai hakan ba dan yanzu hatta security ɗin gidan na ƙofa Alh. Sulaiman ya canja shi, idan zata fita dole saita kira Dada ita kuma ta kirashi sai yasa a buɗe. Gefe guda ga cid ko bodyguard zata kirasu ma ita bata sani ba yasa suna bibiyar al’amarin ta. Ta fahimci hakanne a randa sukai fita yin wani shopping ita da Ummita. Hankalinta ya ƙara tashi, dan zuciyarta zuwa yanzu ta fara ayyana mata abubuwa da dama. Cikin harda tunanin anya kakar tata da kawunta basu da wata manufa a kanta. Wannan shine mafarin data fara natsar da zuciyarta waje guda da hankalinta domin fahimtar abubuwa a matsayinta na lawyer. Abu na biyu shine randa ta amshi wayar Ummita da nufin kiran Daddy a karo na farko. Dan ita nata wayoyin ma ta mantosu a Nigeria tun sanda ta taho, tanata ma Dada naci akan a kawo mata sai taita cewa ta manta. Koda Lulu ta saka number Daddy ta kira sai taji Alh. Sulaiman ya ɗaga. Hakan ya ɗaure mata kai akan miya kawo wayar Daddy hannun Uncle ɗin nata, amma sai ta tsinkayi Alh. Sulaiman ɗin na ƴar dariya da faɗin,……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 🔟
__________________
……..“Karki cigaba da wahal da kanki wajen kiran kowa da wayar nan Mawaddat, koda kuwa Dada ce. Dan duk wanda zaki kira ni ne zakiji na ɗaga, dan lokacin da zasu san ina kiken baiyi ba”. Da ga haka ya yanke wayar ya barta da baki a sake. Na uku har gida ake kawo mata kayan shaye-shaye sai dai yanzu bata iya sha, kallon magani kawai ma tayar mata da zuciya yake yi, jima take ta tsani koda ganinsu. Na ƙarshe shine rashin dawowar Dada Canada tun tafiyarta kusan wata uku kenan. Idan sunyi waya kuma sai tace mata zatazo uziri ne ya riƙeta. Tajuddeen na zuwa gidan kusan duk bayan kwana biyu. Amma ko kallo bai isheta ba. Dan in yazo idan zai yini mata magana ko a bata furta masa har ya gaji ya tafi. Daga baya ma sai ta koma duk randa yazo kulle kanta take a ɗaki har yabar gidan baya ganinta. Duk da yanda waɗan nan abubuwan ke mata kai kawo a rai sai yanayin canjawar jikinta yafi komai ɗaga mata hankali. Da gaske fa komai nata ya canja, tayi ƙiba hallitun jikinta sun sake cikowa, ga wani mugun fresh da tayi kamar ka taɓata jini ya fito. Sai period ɗinta, duk da dama tun kan tai aure yana mata haka tai wata uku bata gani ba, idan kuma zai zo tasha wahalar ciwon mara. Tasha ganin doctors akan matsalar amma amsa ɗaya take samu shine yanayin halittar tane kawai haka lafiyarta lau. To amma a wannan karon idan fa zatai lissafi kusan watanta biyar kenan batayi ba, sai jinin data zubar na lokacin da su Dada suka zubar mata da ciki. Ganin al’amarin na neman sakata a wani hali ya sata saka Ummita ta kira mata Dada. Dada da har yanzu basu koma Nigeria ba sai dai suna shirye-shiryen hakan cikin mamaki take sauraren Lulu dake mata bayani akan rashin ganin period ɗintan. Amma ganin yanda Lulun ta tada hankalinta sai ta shiga kwantar mata akan ta bari zata turo mata Dr Olivia ko kuma ta shirya suje asibitin su sameta. Ɗan son fita da take ne yasata cewa gwara su sametan to. Sai Dadan tace to bari ta samu Alh. Sulaiman da maganar. Kasa shiru Lulu tai ta jehoma Dada tambaya akan miyasa yanzu komai nata sai Dada tace sai Uncle Sulaiman ya sani. Ita kanta Dada sai hakan ya tsikari zuciyarta, rashin sanin ƙwaƙwƙwarar amsa ya sata faɗin Lulun ta bari har sai tazo zasuyi wannan maganar. Badan Lulu taso ba tayi shiru.
Sunje asibiti sun sami Dr Olivia, inda akaima Lulu gwaje-gwaje da duk suka dace, babu wani wahala aka gano ciki ɗan watanni biyar a mararta sai dai kwanakin sa sun ɗan koma baya kaɗan, hakan kuma nada nasaba da yunƙurin zubar da shi da akayi kenan. Ba Lulu ba hatta Dr Olivia ta shiga ruɗani, dan al’amarine da bata taɓa cin karo da shi ba. Saboda tabbas ita shaidace sun zubar da cikin Lulu, sun kuma tabbatar da hakan, amma a yanzu ace musu kuma a kwai shi gashi yana rayuwa cikin ƙoshin lafiya. Dada ma da taji al’amarin hankalinta ya tashi, ta kira Alh. Sulaiman a rikice ta sanar masa. Tamkar wani sumamme haka ya daskare a waje ɗaya, har Hajiya Turai mahaifiyar Tajuddeen da suke tare a lokacin na tambayarsa ko lafiya? Bai iya cemata komai ba face furzar da wata irin iska mai zafi daga bakinsa ya miƙe ya fita. Kaɗan ta taɓe bakinta tare da binsa da kallo, gaba ɗaya kwanakin nan ta gagara gane kan mijin nata, iya tambaya da lallaɓa tayi shi kuma ya dage mata akan babu komai…..
Wani irin rikicewa da daburcewa Dr Olivia tai lokacin data juyo sukai ido huɗu da Lulu da bata san tana bayanta ba. A yanda taga Lulun kuma ya tabbatar mata taji wayar da tai da Dada. Cikin harshen turanci take ma Lulu magana harshenta na sarƙewa. Hannu Lulu ta ɗaga mata kawai alamar bata son jin komai, daga haka ta bar wajen cikin tangaɗin hajijiyar da take ji na kwasarta. Amma koda ta fito sai ta sauya yanayinta saboda bodyguard ɗin da Alh. Sulaiman yasa suke biye da su. Magana taima Ummita akan tazo ta rakata restroom. Ganin ɗaya daga cikin b.g ɗin na ƙoƙarin biyosu ta kallesa sheƙeƙe da faɗin “Can ɗin ma sai ka bimu. Ko an faɗa maka ma na gama abinda nake a asibitin!”. Tsayawa yay kansa a ƙasa dan ya fahimci masifar Lulu tafi tashi.
Tsaki taja da sake ɓalla masa harara sannan taja hannun Ummita. Ba restroom ɗin suka shiga ba, da ga can gefensa suka tsaya, karo na farko a rayuwar Lulu da taji ya cancanta ta sanarma wani damuwarta, dan zurfin ciki babbar ɗabi’arta ce shiyyasa abubuwa da yawa sukai mata nauyi a zuciya.
“Ummita so nake na gudu”.
“Sosai Ummita ta waro idanu waje, sai kuma ta kalla inda Bodyguard ɗin nan da Lulu bata lura ya dai biyosun ba a laɓe, ƙasa Ummita takai kamar mai son gyarama Lulu takalmi, dan Ummita wayayyar mace ce da taga jiya taga yau, hasalima tashin ƙauye ce ita, daga baya ta dawo wajen yayarta a cikin Kano, sai dai matsalar data fuskanta ya sata komawa Abuja a yanzu.. “Aunty karki ruɗar da kanki dan munafukin nan ya biyo mu. Muyi tamkar takalmin nake gyara miki”. Lulu ta fahimceta dan haka hankalinta ya sake tashi. Amma sai Ummita ta ce, “Karki tada hankalinki zamu samu mafita. Aunty tsakanina da ALLAH nake jin ƙaunarki a cikin raina, saboda kin min abinda bazan taɓa yarda a cutar dake ba. Nima halin da kike a cikin gidan nan na tada min hankali. Na kasa tunkararki da batunne saboda ina jin tsoron karki kasa fahimta ta. Sannan ke kanki kin kasa gane tamkar anyi kidnapping ɗinki ne anzo an ajiye anan. Dan gaskiya akwai manufa a al’amarin kawun nan naki a yanda nake lure da shi, na fahimci hakanne tun sanda aka zubar miki da ciki da ɗauke passport ɗin mu da yayi”.
Lulu dake jin hawaye da wata matsananciyar tsanar Alh. Sulaiman ta cika mata zuciya ta ce, “Nima na fara jin haka a raina Ummita, sai dai gani nake mizaisa Dada a matsayinta na grandma ɗina ta aikata hakan, shiyyasa kawai nake hora zuciyata da ƙin yarda. Amma a yau zuciyata ta kasa karɓar al’amarin, cikin da suka zubar ashe bai fita ba”.
Da sauri Ummita ta ɗago tana kallonta. Lulu ta gyaɗa mata kai alamar tabbatarwa, “Yana nan Ummita, kuma wlhy naji ina matuƙar son sa. Idan har kakata nada manufa a kaina itada Uncles ɗina dama family ɗina duka ashe bani da babban abinda ya kamata na runguma sama da wannan cikin, yafi kowa kusanci dani a yanzu, banda uwa, banda ƙani, banda yaya. Daddy na da Uncle Yousuf sun fifita soyayyar wani a sama da tawa. Wlhy a yanzu-yanzu Ummita naji ƙauna da soyayyar abinda ke cikina harda zumuɗi da fatan zuwansa duniya lafiya, a wannan karon bazan bari su taɓamin shi ba, ina son na rayu da shi, bana son na rasashi ko shi ya rasani kamar yanda na rasa mahaifiyata”. Sosai Ummita taji itama hawaye na cika mata ido. Miƙewa tai tana murmushin yaƙe dan har yanzu munafukin na laɓe, sai dai bazai iya jin abinda suke faɗa ba. Hanya ta nunama Lulu alamar su koma tana ɗan murmushin yaƙe. “Muje restroom ɗin karsu fahimci wani abu, ina son ki kwantar da hankalinki ko’a fuska kada ki nuna musu kina son cikin balle yunƙurin guduwa. Na miki alƙawarin kozan rasa raina zan taimakeki. Dan nima kin min abinda bazan taɓa mantawaba, wanda shine dalilin amsar wannan aikin da nayi a lokacin da na ganki cewar kece wadda zan zauna da ita anan”. Sosai Lulu kema Ummita kallon mamaki, amma sai Ummitan tai mata murmushi kawai. Restroom ɗin suka shiga, Lulu ma sai tai fitsari sannan suka fito. Ganin sun nufo hanyar dawowa bodyguard ɗin nan yay saurin yin baya yana sanarma Alh. Sulaiman cewar gasu nan zasu dawo da gaske restroom ɗin suka shiga. Sarai Ummita taga waya a kunnesa, hakan ya sata sake gaskata zarginta. Sun koma wajen Dr Olivia wadda suka sameta tana waya da Dada. Dan haka Lulu ta laɓe tana saurarenta. Dr Olivia da bata lura da Lulun ba ita cikin harshen turanci ta cigaba da faɗin, “Idan akace sai an fidda cikin nan a wannan gaɓar akwai babbar matsala, dan za’a iya taɓa lafiyar ta ɓangarori da dama, koma a rasata baki ɗaya. Kawai Mrs Garko kuyi haƙuri ta haifi abinta. Amma dai har na mutu bazan daina mamaki da al’ajab ɗin wannan al’amarin ba, harma na sakashi a cikin manyan record namu na ban mamaki da suka faru a asibitin nan. Sannan zanyi bincike mai ƙarfi akai dan tabbatar da daga ina aka samu matsalar”.
Shiru alamar tana sauraren Dada itama, sai kuma ta nisa da cewa, “Shike nan sai kin shigo ɗin”. Daga haka ta yanke wayar. Haɗiyar zuciya Lulu ta dingayi cikin wani yanayi, kafin ta saita kanta da ƙyar ta nufi cikin office ɗin. Murmushin da Dr Olivia ta gani a fuskar Lulu ya ɗan sata jin relief, ta rubuta mata magunguna da abubuwan da ya kamata taci dan inganta lafiyarta data abinda ke cikinta. Lulu tai mata godiya ta fito akan zata cigaba da zuwa awo. Koda suka fito a asibitin sai da suka tsaya sukai ɗan shopping sannan suka wuce gida. Sun samu Tajuddeen yazo, amma kamar yanda Lulun ta saba kallo ɗaya ta masa ta kauda kanta tare da wucewarta ɗaki tana amsa masa gaisuwar da yake mata a taƙaice. Tajuddeen da yake jin kamar ya fasa kuka ya sauke numfashi mai nauyi tare da dafe saitin zuciyarsa dake harbawa da sauri-sauri, da gasken gaske yake ƙaunar Lulu, soyayya yake mata mai zafi wadda shi kansa wani lokaci yana jin abun na neman fin ƙarfinsa. Bai taɓa jin koda ɗigon sonta ya ragu masa a rai ba duk da cin kashin da take masa. Hasali ma duk abinda tayi sai ya zama shi birgeshi take yi tare da ƙara jin sonta a ransa. Burinsa ya mallaketa matsayin matar aure, ta zama uwar ƴaƴansa, randa yaji ta ɗauki cikin wani ba nasa ba har hawaye yayi, dan ƙarshe ma sai da ya ga likitansa………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣1️⃣
…….Kasancewar Tajuddeen a gidan ranar ya hana Ummita da Lulu sakewa, dan itama dai Ummitan irin mutanen nan ne masu tsantseni akan addini da rayuwa, balle kuma itama ɗin dai tanada tabo irin na Lulu, koma muce ya zarce na lulun tunda ita an riga an keta mata nata mutuncin a sanadin fyaɗen ma harta haifi ɗa sai dai a yanzu babu shi a raye, abin takaicin kuma mijin yayarta data riƙeta ne wanda ta taso tanama kallon tamkar uba ta aikata mata hakan. Sannan tanada matuƙar wayo da lura akan al’amura na rayuwa. Lulu data rufe kanta a ɗaki saboda kasancewar Tajuddeen ɗin tana shiga saman gado ta kwanta tai shiru cikin nazarin abubuwan da suka faru a yayin fitar tasu yanzu. Sai kuma kamar wadda aka tada ta tashi zaune zuwa gaban mirror ta nufa, kanta ta ƙurama ido na tsawon lokaci, kafin takai hanunta ta ɗage rigarta gaba ɗaya ta ƙurama cikinta da ya ɗan turo kaɗan idanu, sai kuma ta kai hannunta saman shi a hankali ta lumshe idanunta hawaye na ciko mata su, ɓul-ɓul taji ya harba tamkar abin shiri, da sauri ta buɗe idonta da hawaye suka cika taf tana kallon saitin daya motsa ɗin, sai kawai ta saki dariya mai haɗe da kuka. Dan abu uku ne ke mata kai-kawon. Wai ita Mawaddat Isma’il Ibrahim Jiƙamshi ce ɗauke da ciki na haihuwa, abinda bata taɓa kawowa a jerin tunaninta ba na rayuwa. Duk da kuwa tanada masifar son yara a rayuwarta, amma bata taɓa kwatantasu gareta anan kusa ba ace matsayin ga nata ba a dalilin tsanar maza da tayi a rayuwarta. Sai kuma wata hikima ta UBANGIJI da ikonsa gashi a yau itace aka tabbatarma zata haihu ɗan mutum matsayin mallakinta. (Mallakinku dai ke da ubansa) wata zuciya ta ayyana mata. Idanunta dake a rufe tai saurin sake buɗewa, dan abinda zuciyar tata ta tsikaro mata yay matuƙar dakar ƙirjinta. (Aliyu) ta sake ayyanawa a zuciyarta tare da kaiwa zaune a kujerar mirror ɗin tamkar cikin gajiyawa. Sai kuma a fili kamar wadda aka tunzuro ta furta, “Ai har abada bama zai san da cikin ba balle zuwansa duniya ko rayuwarsa Mtsowww!!” ta miƙe a ɗan hasale. Kokawa ta shiga yi da zuciyarta akan abinda take ta ƙoƙarin sake tsikaro mata game da Smart ɗin. Cikin tsawa-tsawa kamar zararra tace, “Please and Please bana son damuwa a beg”. Ta ƙara jan tsaki ta shige toilet. (Ni sai ma taban dariya sai kace wadda keyi da wani a gabanta😂🤳).
A haka Lulu ta ƙarasa wannan yini cikin wani irin yanayi mai wahal fassara a gareta ita kanta. Sai dai jaɗan-kaɗan hannunta na saman cikinta, yayinda zuciyarta ke cigaba da kawo mata al’amari mai nauyi dangane da kakarta da kawunta da sukaso rabata da shi batare da ko sau ɗaya sun taɓa tunkararta da batun tana da ciki ba ko tunanin zata so abinta. A ganinta wannan babban taka hakkin ɗan Adam ne ai, sannan bataga minene dalilinsu na zubar mata ɗin ba. Dole tana son tasan dalilinsu musamman ma Uncle Sulaiman data rasa dalilinsa na shishshigema rayuwarta a yanzu. Tunda a baya ita dai takan ma haɗa watanni bata ganshi ba. Ganin damuwa na neman cinkushe mata rayuwa ga kayan shaye-shaye sun gagareta sha a yanzu balle tasha ta manta damuwarta ya sata tattare tunanin ta ajiye gefe. Sai ma wani ɗan murmushin takaici ko damuwa za’a kirashi data saki, tare da shafa cikin nata a fili tace, “Wato kai saika nuna min daga jinin wanda ka fito ko?, abu na farko daka fara datse rayuwata da shi shine shaye-shaye, to ya isa a tsaya iya nan inba hakaba a sha ranƙwashi dan bana son shishshigi, shima uban naka yasan ba kanwar lasa bace niɗin tunda ban taɓa raga masa ba akan shiga min hanci daya dinga yi” ta duddungure cikin da yatsanta, zafin da taji ya sata ɓata fuska da sake faɗin, “Garama ka biyo halin Ammah dai zan iya fatan haka ba wannan mutumin mai fuska a turɓune ba uwa ta shanu” daga haka ta fito zuwa falo, dan tasan dai Tajuddeen ya wuce ai yanzu. Ilai kuwa Ummita kawai ta samu a falon tana ƙara gyarawa. Cikin ɗan murmushin da ayau ne ta fara yinsa ga Ummitan ta ce, “Ɗazun mun fara magana amma baki ƙarasa bani labari ba”. Ɗan kallonwa Ummita dake murmushi tayi, sai kuma cikin yanayin signal da idanu ta mata nunin tai shiru da bakinta. Sarai Lulu ta fahimta kuwa, dan haka ta waske da cewar, “Yanzu ni kuwa dama labarin ko dai film ɗin zan nema kawai na kalla da idanuna”.
Murmushi mai ƙayatarwa Ummita tayi tare da jinjina a kaikaice ganin uwar ɗakin nata ta fahimci abinda take son ta fahimta ɗin cikin sauri, dan haka itama ta fara bata labarin wani Hausa film da take kallo a YouTube kawai. Sai daga baya Ummita ta ajiye mata ƙaramar takarda. Ɗauka Lulu tayi tana dubawa dan cikin littafi ta saka mata yanda ba za’a gane ba.
_“Aunty dole fa sai munyi taka tsantsan, dan inaji a jikina an saka mana recorder a cikin gidan nan da take recording duk wani magana da muke iyayi koda bata shafi komai ba, maybe ma harda cctv camara”._
Lulu ta jima tana kallon takardar da Ummitan ta ajiye tare da shiga dogon nazari akan abinda tace ɗin dama abubuwan dake faruwa. Wanda ya kamata dama tun farko ta nazarcesu a matsayin ta na Lawyer. Sai dai rashin fahimtar dalilan da zata iya hangar abubuwanne kawai yasa bata kai can ɗin ba, da kuma halin rashin lafiyar da take ciki shima. Zaram ta miƙe daga falon zuwa bedroom ɗinta, tamkar wadda akaima allura ta fara kaikawo tare da tsunduma cikin gidauniyar nazari. Komai take bi dalla-dalla, tun daga randa Dada ta ɗakko ta da ga gidanta har zuwa zamanta Abuja na kwana biyar a hannun Hajiya Shuwa batare da Dada ta barta ta nufi gidan Uncle ɗinta Khamil ba. Zuwansu Canada da kai-kawon da Uncle Sulaiman keyi anan ɗin shi da Tajuddeen. Yunkurin zubar mata da ciki da ɗauke mata passport da yayi daga ita har Ummita, bibiyar ta da taga anayi da canja security ɗin ƙofar gidan da akaiyi da bata isa fita ba daga ita har Ummita sai da izinin Dada, amma kuma ai shi Tajuddeen kai tsaye yake zo musu. Maganar da Dr Olivia tayi yau da Dada, zancen Ummita akan recorder da cctv camara da take hasashe. Tsaf Lulu ta haɗe waɗan nan abubuwan waje guda tare da tattara hankalinta a jikinta ta saka rigar lauyanci. Tana zaune a gado pen da book a hannunta tana rubuce-rubuce akan haɗa wancan da wannan ya bata ma’ana Ummita ta shigo ɗakin da sallama ɗauke da kofin kunun gyaɗa da ya zama abincin Lulu. Sai tururi yake da ƙyamshi mai daɗi. Ummita ta ajiye mata saman coffee table da ɗan kaiwa tsugunne a gabansa ta fara tsiyaya mata a ƙaramin kofi. Cikin raɗa-raɗa ta ce, “Aunty karfa ki tada hankalinki akan maganar nan da kikaga na rubuta tunda bawai mun tabbatar bane ba ko gani da idonmu. Amma ina son daga yanzu mu sake taku a gidan nan musamman akan wannan cikin na jikinki. Aunty duk da ban san miye dalilin son zubar da shi da ake ba ina son ki gane muhimmancinsa a gareki kamar yanda kika faɗa a ɗazun. Dan da ace bai kasance mai muhimmanci ba baza’aita kawo masa hari irin haka ba na san salwantar da shi gaba ɗaya. Sannan ina son ki nutsu a matsayinki na lawyer ki fahimci wanene kawunki da ɗansa da manufarsu, dan tabbas a nawa guntun nazarin na fahimci kamarfa suna amfani da Dada ne kawai a wannan al’amarin, kai shi kansa Tajuddeen ɗin kamar uban amfani yake da shi a kanki kawai wlhy”. Tunda Ummita ta fara magana Lulu ta zuba mata idanunta ne kawai. Dan gaba ɗaya lissafin Ummitan yazo dai-dai ne da nata. A hankali itama ta furta “Ummita duk ya akai kika san wannan?”. Murmushi Ummita tayi da ya ƙara fidda ƙyawunta da gogewar data sake yi na zama a turai. Cikin nisawa ta ce, “Aunty kenan. A kanki zan iya yin fiye da hakan, dan ke wata madubi ce ta rayuwata data haska min kaina da ga ruɗanin munana zuwa na MACE MUTUM mai daraja”. Hannu takai ta share hawayen da suka sakko mata, sai kuma tai murmushi mai ciwo. “Aunty ki bari zamuyi magana amma ba’a gidan nan ba, sai dai ki yarda aikine tuƙuru a gabammu wlhy, amma bana son muyisa cikin gaggawa in har muna son kuɓuta da ga wannan tarkon cikin ƙoshin lafiya batare da an rasa wani a cikinmu ba.” ta miƙe a hankali ta nufi ƙofa. Da kallo kawai Lulu ta bita cikin wani irin yanayin sake shiga firgici, dan har wata ƴar zufa-zufa ke tsatstsafo mata a goshi. Sai kuma ta lumshe idanunta dai-dai sanda Ummita take ficewa a ɗakin gaba ɗaya ta zame ta kwanta. A karan farko ta saki lallausan murmushi irin wanda ke tabbatar da Lulu ƙamshi ta dawo kenan da ga barcin daya figeta na wucin gadi ba Mawaddat ta yanzu ba mai yawan karaya da yin sanyi. Dan tabbas a yau Ummita ta zame mata tamkar wata fitilar tochlight data haska mata wajen ajiye ƙafa da ɗaukewa, sannan allura mai ƙarfin gaske da ta zaburar da ita tare da wanke mata idanunta da ke lulluɓe a ɗan watannin nan cikin yanayin barci ruɗani. Laulayin cikinnan da daina shan abubuwanta ya so maidata wata sabuwar Mawaddat ba Lulu ƙamshi ba. Idanunta ta sake buɗewa a hankali ta ƙure p.o.p ɗin ɗakin da kallo. A zuciyarta ta ce, (Tabbas Ummita gaskiya kika faɗa, yanzu ba lokacin gaggawa bane ko burin guduwa. Lokacine na cigaba da kwantar da kai matsayin MAGE MAI KWANCIYAR ƊAUKAR RAI har sai nasan SIRRIN DAKE ƁOYE. Dolene na fara sanin manufar Uncle Sulaiman a kaina tare da tantance Dada kafin a fara wasan) ta saki wata ƴar siririyar dariya da faɗin,
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣2️⃣
………*_LONDON_*
A kwana a tashi ba wuya wajen UBANGIJI. A ɓangaren Smart komai na tafiya dai-dai da fatansa dama na duk masoyansa. Sosai ya ƙara canjawa a komai na halittar jiki, gogewar fatarsa da sake zamansa tsayayyen namiji ƙyaƙyƙyawan, ƙiba dai kam bai ƙara ba, sai ma canji wajen zama dana abinci da ya saka shi ɗan ramewa kaɗan dan yasha wahala kafin ya saba ci, yanayin ramar tasa sai ya sake fidda masa ƙuruciyarsa. Harma wani zai iya ɗauka shekarun da yake amfani da su a ƙwallon sune nasa na gaskiya. Kamar koyaushe Lulu na nan daram a ransa, sai dai ɗammarar da ya ɗaura akan tattara al’amarinta da duk wani wanda ke kusa da ita ya sashi dakewa tamkar a yanzu babu komai dake gaban nasa sai harkar ƙwallo da ibada da sam baya sakaci da ita. Abu ɗaya ke damunsa a kanta shine duk dauriyarsa a kowane dare kafin barci ya ɗaukesa daren nan mafi daraja daya ratsa a tsakaninsu ya dinga masa kai-kawon kenan, wataran har takan kaisa ga mafarkinta a wannan yanayin har sai ya kaisa ga wanka kafin sallar asuba. Wani lokacin kuwa har mafarkin gasu a tare yake da ciki a jikinta kotana shayarwa. Duk randa yay irin mafarkan nan yakan tsinta kansa a cikin nishaɗi duk da yana ganin abune mai wahala da yuwuwarsa ba lallai ba, bai kuma taɓa hasashen zata iya kasancewa da cikin na a haɗuwarsu ɗaya kacal, dan duk da ƙarfafashi da zuciyarsa da su Ammah keyi baya jin hasashensa zai iya tabbata akan sake kasancewar su inuwa ɗaya da ita balle har a kai ga haihuwa kuma. Dan ya jima da fahimtar Lulu nada taurin kai dana zuciya matuƙa akan abinda take ƙi ko take so….
A yanzu haka su Smart sun fara wasan da suka kwashe tsahon watanni suna training akai. Wasane da gaba ɗaya ƙasar Unitet Kingdom hankalinsu ke akansa, kasancewar ya shafi kowa-da-kowa. _Smart Mawashi no. 9_ da ya kasance wannan ne wasanshi na farko a cikinsu tun a wasan farko ya fara bada mamaki. Inda ya zama mutum na farko da ya jefa ƙwallo a raga. Ba’a ɗauki dogon lokaci ba ya sake na biyu. Babbar magana kenan, dan kuwa fa a wannan rana gidajen jaridu da na tabijin harma da rediyo da yanar gizo na ƙasar ta UK a duniyar ƙwallo ka-ce-na-ce ake akan wannan sabon yaro na Queen City, dan ya girgiza zukata fiye da tunani. Farin ciki da Coach ɗin su ya shiga tare da Teammate ɗinsa da fans a wannan rana ba’a magana. Shi kansa yana cikin farin ciki mara misali, dan daga ƙwallon farko har ta biyu da ya jefa sai da yay sujida wa UBANGIJI. Bayan gama Home mach da sukaci 3-1 sati mai zuwa suka tafi away mach, a wannan rana ma al’amarin sai godiyar ALLAH, dan ranar ma dai Smart ya zira ƙwallo sau ɗaya duk da dai ansha wahala matuƙa da gumurzu. Tofa, abinfa ya fara zama babban al’amari. Dan al’amarin Smart Mawashi ya fara ratsa zukatan turawan ƙasar England. Wasan link ya cigaba da tafiya fiye da yanda Smart ke fata, dan matuƙa team ɗin nasu na taka rawar gani, saboda sune na ɗaya a tebiri, dan sunada maki kusan talatin da biyu, sun kuma bama team dake bimusu tazarar kusan maki goma sha biyu. Suna taka rawar gani ta yanda a duk randa zasu buga wasa zakaga stadium ɗin ta cika maƙil fiye da kowace rana. Smart ya jefa ƙwallaye goma a wasa goma sha biyu da suka buga, sunci wasa goma, sunyi drow a biyu. Haka dai wasa ya cigaba da tafiya cikin nasarori daban-daban tare da ƙalubale. Ranar da za’a buga wasan daya kasance kamar na dabi ko hammaya tsakaninsu Model Unitet cika iya cika stadium ɗin tayi. Dan duk wani masoyin ƙwallo na ƙauye dana birni a wannan ƙasa dama maƙwaftan ƙasar sun taru domin ganin wannan wasa na da sabon ɗan wasan dake lokaci da Queen City zata buga da Model Unitet ɗin da kowa yasan akwai hamayya mai ƙarfi tun shekarun baya tsakanin team ɗin guda biyu. Bayan kammala al’adu irin na ƴan wasa su Smart suka shigo cikin fili. Bakinsa ɗauke yake da addu’a kamar kullum, yayinda yake sake jin wani irin karsashi da himmar ganin yanda ya tara masoya a ƙasar daba tashi ba. Wasa ya fara gudana yanda ya kamata, sai dai a mamakin kowa yau Smart sai wani jan jiki yake yi, gashi shine lamba tara da kowa zai iya taɓawa. Kaɗan-kaɗan masoyansa dama na team ɗin sa suka fara ƙananun maganar yau kuwa lafiya?. Shi kansa Coach nasu hankalinsa ya fara tashi ganin yanda Smart ke gara ƙwallon a kasalance, sai dai abin jin daɗin sun tare ko’ina har yanzu suma abokan hamayyar tasu basu zira ƙwallo ko guda ba, sunata dai kai hari. A haka har aka je hutun rabin lokaci babu wanda ya zira ƙwallon. Dabaibaye Smart da tambaya Coach yayi akan ko baida lafiya ne yau. Amma sai yay murmushi ya ce lafiyarsa ƙalau kawai dai a haka wasan yazo. Sake jan hankalinsu Coach yay akan karsu bari suyi wahalar banza bayan nasarorin da suka kwararo a baya, saboda in har suka bari Modal Unitet sukaci galaba a kansu zasu sanyaya gwiwar masoyansu ne, dan shi dai yau bai gane komai ga Smart ba. Tofa wasa ya canja salo, dan ana dawowa kowa ya nuna da zafinsa ya dawo. A mamakin kowa sai akaga Smart ya ware kamar bashi ba. Abinka da rainon gero da masara a tsaye yake kan ƙafafunsa babu jin gajiyawa ko nuna rauni, gara ƙwallo yake a fili da iyakar ƙarfin zuciya dana ƙwanji. Cikin mintuna biyu da dawowa su Smart suka zira ƙwallo ɗaya, sai dai bashine ya zira ba. Wannan zira ƙwallo ya sake saka wasan ɗaukar zafi suma Model Unitet team ɗin suka rama a mintuna goma da dawowa. Tamkar an tsirama Smart allura ne shi da Teammate na shi a wannan gaɓar. Bata kashi ake na gaske kowa nason ganin ya sake nasara da kai ɗan uwansa ƙasa, amma hakan bata samu ba sai a kusan mintuna ukun ƙarshe da za’a tashi cikin amincin ALLAH Smart ya saka ƙwallo a raga. Wani irin ihu stadium ɗin ya ɗauka tamkar garin London zai tsage kasancewar yau wasan na cikin gida ne, dan Model Unitet ɗin suma ƴan nan cikin London City ɗin ne. Sakanni ashirin da huɗu saura Smart ya sake jefa ƙwallo ta biyu uku kenan da ɗaya. Ya arrahaman zokaji yanda stadium ɗin ke girgiza saboda matsanancin ihu da masu kallo suka ɗauka. Yayinda teammate ɗin Smart suka wani irin rungumeshi a tsakkiya bayan ya ɗago daga sujidar daya zube ƙasa ga hawayen farin ciki sun wanke fuskarsa. Dolene yay farin ciki, a cikin mintina ukun ƙarshe saura a tashi kacal da kowa ya gama fidda ransa za’a tashi 1-1 amma ya zira ƙwallo har sau biyu, wannan abun yayi kukan farin cikine tabbas..
Wannan itace mafarin nasarar tabbatuwar cikar mafarkin Smart a harkar ƙwallon ƙafa. Dan gaba ɗaya ƙasar England da kafafen yaɗa labarai suka ɗauka. Tako ina ƙasar ta ɗauki zance akan wannan sabon yaro da Queen City ta samo a wannan karon. Wanda daga fara wasan link zuwa yanzu ya zira ƙwallaye ɗai-ɗai har goma sha uku kenan. Wannan nasara bata tsaya a iya ƙasar UK ba, hatta da sauran duniyar ƙwallo ma ta kurɗa a cikin labarai dama masu bibiyar wasanni. Inda masana ƙwallo keta ƙara fashin baƙi akan _Smart Mawashi_. Dan al’amarin ya girgiza mutane da yawa kasancewar wannan shine farkon wasan link daya buga a ƙasar ƙetare bayan na ƙasarsa Nigeria a baya. Coach Abdull-Hameed da takanas ya tafi ƙasar England ganin wannan wasa na su Smart yau saboda yanda yake ta nuna musu fargabar yinsa a dalilin jin labarin su waye Model Unitet ɗin shi da Uncle Yousuf da Ahmad harda hawayensa. Yana jin alfahari da kasancewar Smart rainonsa ne. Yayinda shima Smart kejin alfahari da hakan. Koda sukai waya da Ammah sai kawai ya sakar mata kuka. Ita sai ma abin ya bata dariya. Duk irin kafiya ta Aliyunta da taurin zuciya kaga yana kuka ai wannan al’amari ya kai babba a jerin farin cikin sa ko damuwa. Wannan dai tasan na farin ciki ne. Addu’a ta dinga jera masa daga ita har Abba duk da sudai ba sanin kan abun sukai ba…..
A yau wayar Smart da Abbah ita ta haskakama matan gidan mi ake ciki, dan Umma na tare da shi ne a sanda Smart ɗin ya kira sa kasancewar itace da girki yau ɗin. Ƙagara tai Abba ya gama wayar jikinta har karkarwa yake ganin numbar da aka kira Abban kuma taji ya ambaci Aliyu ta fara da +44.. yana gamawa cikin rawar harshe ta ce, “Alhaji wai wane Aliyu kuma ka samu da lambar wajen ƙasar nan haka?”.
Kai tsaye cikin rashin damuwa Abba ya bata amsa da cewar, “Aliyu na ma. Ai yana can ƙasar turawa buga ƙwallo. Yanzu haka ma ya kirani ne yana faɗa min sunci wasan da tun kusan kwana biyar kenan yake faɗin mu tayasu da addu’a akai dan wasan nada ƙalibale sosai. To Alhamdullah sunci kuma shine ya saka kwallon har sau biyu bayan har sun fidda rai ga hakan”.
“Tofa sabon zance, shi Hydar ɗin ne ya tafi ƙasar Turai ƙwallo amma mu da muke a gidan bamu da labarin hakan? To Alhaji wani sabon makirci ne yazo ake ɓoye mana hakan kamar wasu masu baƙin ciki ko mugun hali ko yaya ne!!?”. A hasale Umma ke magar har idanunta da suka kaɗa jajur na tara ƙwalla.
Abbah da sai yanzu ma shi ya tuna cewar babu fa wanda yasan ina Aliyun yake bayan shi da Ammah da Bilkisu ya tsurama Ummah idanu da mamakin ganin yanda take kumfar baki. Sai dai maimakon ya mata masifa kamar yanda ta hayayyaƙo masan sai yay yinƙurin son fahimtar da ita dalilin ɓoyewar tasu cikin hikima. Amma abin mamaki Ummah ta birkice masa cikin ɗaga muryar data jawo hankalin jama’ar gidan gaba ɗaya zuwa sashen Abbah. Tun Umma na jidali da Abba a ɗakinsa har fa ta fito tsakar gida ta maida abin kan Ammah. Nanfa Mama itama ta ara ta yafa jin ba’asi, yayinda samarin gidan da sauran yaransu suma dai maganar tai mugun dukansu. Ammah dake da ga falonta zaune shiru kawai tai tana sauraren jidalin da Umma da Mama keyi, sai aunty Amarya dake basu haƙuri da faɗin ita bataga abin tada jijiyar wuyaba anan, kamata yay a kwantar da hankali aji dalilin su Abban nayin haka dan bazasu ɓoye ba ai da gangan dole suna da dalilinsu. Neman dawowa faɗan yay akan aunty Amarya, suna cewa itama ai munafukar ce, tunda tana naniƙe a jikin Ammah dan ƙwaɗayin ganin ƴaƴanta na auren masu kuɗi dole tace haka. Maybe ma tasan da tafiyar Aliyun amma taja bakinta tai shiru saboda makircinta da munafurci. Aunty Amarya kusan halinsu ɗaya da Ammah, itama bata da faɗa sai in an kaita maƙura, dan haka tai musu shiru da ga farko, sai da taga suna neman keta mata mutunci a gaban yaransu itama ta fara zazzaga musu nata masifan. Nan fa gida ya sake harmutsewa har sai da Abbah ya fito da ga ɗakinsa a fusace…….✍️
_🥱Shin Hajiya Yahanasu babu rami miya kawo rami ne?._
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣3️⃣
……..Cikin rufewar ido da nuna ɓacin rai Abba ya tsawatar musu. Ganin Umma na gunguni ya ce, “Wlhy duk wadda ta sake cewa tak sai ta bar min gida a wannan daren. Kuna son maidani wani shasha ne? Kuje an ɓoye muku tafiyar Aliyun kuyi duk abinda kuke jin zaku iya yi dan ALLAH marasa mutunci kawai”. Da ga haka ya koma ciki fuuu ya barsu da harare-harare. Duk abinda akeyi Ammah na jiyosu amma ko leƙowa batai ba, ta kuma hana har su Asma’u leƙowa wajen. A haka aka kwana cikin ɓacin rai wannan dare. Tun kuma a daren su Umma suka bazama sauran ƴaƴansu bayani ta waya cikin nuna hassada. Haka ma ƴan anguwa da rikicin ya ɗan shiga kunnuwansu musamman maƙwafta aka fara riƙe bakin mamakin jin Aliyu ashe baya Nigeria, duk ƙaryar da su Umma keta bazawa matan anguwa cewar ya gudu Lagos saboda dangin matarsa sun ce sai ya saketa ashe ƙarya ce. A wannan dare Umma bata koma ta kwana ɗakin Abba ba, washe gari sai ga yaran gidan na ma’auri nata zuwa musamman mazan tunda safe a cikin tashin hankali. Salim babban ɗan Umma da take ji dashi da fariyyar yafi kowa kuɗi a gidan shine tsageran tunkarar Abbah da maganganun rashin kunya wai yana nuna musu banbanci akan Aliyu. Sai da Abba ya gama saurarensa tsaf sannan ya zageshi ciki da bai da faɗi masa ashe sai yau ne suka san matsayin Aliyu da mahaifiyarsa a wajensa. To bari ya ƙara tabbatar musu da cewar Ammah ta daban ce a zuciyarsa, dan itace first love ɗin sa. Ta auresa a sanda baida komai, yayinda mahaifinta ya tallafi rayuwarsa batare da ƙyama ba a matsayinsa na almajiri, da ya nuna yana son ƴarsa ko sau ɗaya bai nuna ta fisa ba ya aura masa. Tun suna zama a gidan haya ɗaki ɗaya har ALLAH ya horo masa gidan kansa. Ammah tasha rufama rayuwarsa asiri da danginsa da abunta bata taɓa nuna masa isgili da hakan ba koda a cikin wasa. Tayi haƙuri da shi ita da iyayenta akan rashin haihuwa, har sai da uwarsa ta shigo da ƙarfin tuwo ta haifesa shi da ƙaninsa Sadiq kafin ALLAH ya bata cikin Bilkisu. Amma bata taɓa nuna baƙin cikinta ko hassada akan wata tazo a bayanta ta haihu ba. Uwar tasu da suke gani matsayin ƴar uwarsa shi bai taɓa jin sonta ba, da biye-biyen dangi ta kama ƙafa aka tilastashi aurenta… Wannan magana ta Abba taima Umma zafi matuƙa, har ta kaita da fashewa da kukan wai Abba naci mata mutunci a gaban kishiyoyi. Duk da Mama da ita aka fara fitinar sai gashi ta koma yima Umma dariyar ƙeta. Dan ba ƙaramin wankin babban bargo Abba yay mata ba a ranar. Har sai da ta kaita da kuka da hawaye. Da ga ƙarshe ta shige ɗaki ita da ɗiyanta suna zagin Ammah da jawa Smart mugayen addu’oin rashin nasara badan ya musu laifin komai ba sai hassada da uwarsu ta cusa musu kawai a ransu matsayinsa da ɗan uba garesu. Ɓacin rai ya saka Ammah tattara kowa a gidan ta watsar, inda cikin hikima ta nusar da aunty Amarya akan kada ta sake biyema su Ummar dan ALLAH. Tako ji maganarta dan itama ta kame kanta dana ƴaƴanta waje guda kamar yanda Ammah tayi.
Tun a ranar Umma tai kiran Hajiya Naqiba ta sanar mata komai cikin ɓacin rai. Ran aminiyar cin mushen nata ya ɓaci itama. Inda ta balbale Umma da faɗan miyasa ta kasa riƙe kanta ne ta fito tai magana haka har miji na mata tonon silili a tsakiyar ƴaƴa da kishiyoyi maƙwafta na saurare. Cikin damuwa da hawayen da suka cika mata ido ta ce, “Rainane ya ɓaci wlhy Hajiya Naqiba. Kiga wahala da kashe kuɗin da nai akan yaron nan amma sai da ya tafi wannan shegiyar tamaular da na dutse ya tabbatar min itace silar arziƙinsa da bama gidanmu ba hatta ƴan anguwa nan sai ya riƙe da dukiyarsa. Wane irin koma baya ne ya sameni da har haka zata kasance. Wai yaushe ma ƙullin malam Na-zuru ya kwance akan yaron nan?. Haka fa zancen aurensa sai ji kawai mukayi, yanzu dan cin amana da makircin wannan shegiyar matar dake wani sim-sim kamar ta ALLAH za’ace wai yana Turai……”
Ƙaramar dariyar data katse Umma Hajiya Naqiba tayi, sai kuma tai saurin faɗin, “Yi haƙuri wlhy kece kika ban dariya da kikace sim-sim. Bayan kinsan Hafsatu ba sim-sim bace ba kawai dai tana kwasar ƙurarku ne ta watsar. Amma matar da in ta tashi muku wankin babban bargo sai kun kasa sukuni kike jinginawa da sim-sim, kawai dai shegen girman kai ne da ita kamar yanda ɗan nata ya gado saboda taga ta fiku komai. Ubanta mai arziƙi, tanada ƙyau, gata da ilimi kamar zai kasheta duk da ma bata son nunawa…..”
“To wai ni ban gane ba, yabonta kike ko minene?”.
“A’a rufamin asiri, wane yabo zanma kishiya nikuwa. Kinga mubar zancen tunda kin gagara fahimtata. Yanzu dai bamuga ta zamaba kenan. Dan na fahimci makircin da muka ƙullo a gidan Garko ba dukane yay tasiri ba ko kuwa yaya miya faru?”.
“Dan tasiri fa yayi tasiri, tunda gashi har sun ƙwace ɗiyarsu daga hannunsa. Abinda dai zamuyi shine shima fa makircin sai an haɗa mishi da ƙulli….”
“Ƙulli wane iri? bayan wanda mukayi”. Ummah ta katseta da sauri. Ɗan jimmm Hajiya Naqiba tai da faɗin, “Kai kuma fa haka ne, to kodai tsohuwar nan bata bama yarinyar nan rubutun nan ba ne? To aiko da sakel, dan dolene kiyi duk yanda zakiyi a satin nan mu shiga wajen Malam Na-zuru. Dan ba’a bori da sanyin jiki, dolene mu sake tashi tsaye akan wannan ɗan iskan yaron kuwa.”
“A yanzu kam da ya hau sama bana jin zai bar wata fita a gidan, sai dai ki taimaka min kije zan kirashi ta waya mu fara magana kafin kije”.
“Shike nan hakan ma yayi kuma dabara ce. Dan ko wani abu ya biyo baya ma baza’a zargeki ba kamar wancan sai dai suyita tunani cikin abokan tamaular tashi ne”.
Haka suka cigaba da tattauna mugayen ƙudirinsu akan Smart da Ammah iri-iri kamar basa tuna mutuwa mai gaggawa da kan iya ziyartar bawa a kowane lokaci a kowane irin yanayi mala’ikan mutuwa shi mai cika umarnin UBANGIJI ne…….
(ALLAH ka gafarta mana ka tsarkake mana zukatanmu, ka hanamu damar saɓa maka balle ta kaimu ga shirka ko cutar da wani mun akan abinda bazamu taɓa iya sakawa ko hanawa ba.😭🙏)
*_CANADA_*
Dada ta iso ƙasar Canada kamar yanda taima Dr Olivia alƙawari, sai dai a ranar babu damar ganinta dan bata duty kamar yanda ta sanar mata. Kai tsaye gida ta nufa inda ta samu tarba a wajen Lulu ta musamman. Zuciyarta ta mata sanyi ganin yanda jikar tata ta saki jikinta a yau ba kamar yanda suka rabu ba. Sai dai duk motsin Lulun idonta na’a kan cikinta ne, amma batace komai ba dan Alh. Sulaiman yace mata kartace ma Lulun komai har sai ya iso. Tsaf Lulu na lure da ita amma ta basar sai ma tambayoyi data shiga jero mata akan yaya jikin Baba Garko. Dada ta amsa mata da cewar, “Ai jiki yayi sauƙi dan yanzu haka ma an sallamemu muna gida, har shi yana ma batun komawa Nigeria dan ya gaji da zaman turan”. Murmushi Lulu tayi cikin tsokana ta ce, “Dada kawai dai yana son ya gudu ne saboda tsoron kar sanyi ya ƙarasa rugurguza miki shi.” Ranƙwashi Dada ta sakai mata amma sai ta kauce da sauri tana dariya. Haka sukai hirarsu yau cikin nishaɗi har Tajuddeen ya iso. Anan ɗin ma Lulun ta basu mamaki dan bata tashi ba kamar yanda takeyi a duk sanda ya shigo gidan. Koda ya gaisheta ma sai ta amsa masa harda cewa “ykk?”. Duk da ataƙaice ta tambayi lafiyar tasa wani irin sanyi da shauƙi ne suka riskesa a lokaci guda. Ya saki wani irin lallausan murmushi da sauke ajiyar zuciya. Ƴar sakewar Lulun ya sashi kwana a gidan yau, washe gari sun wayi gari da zuwan Alh. Sulaiman tamkar a ƙasar ya kwana. Shima Lulu ta gaishesa sama-sama yana binta da wannan shegen kallon nasa ƙasa-ƙasa. Yayinda shima Tajuddeen ke ɗan binta da kallon mamaki musamman cikinta da yaga ya turo. Dukansu Lulu a hankalce take dasu, dan cikin ma ta saka rigar da zata bayyanashi ne garesu su gani da ƙyau saboda neman magana. Sai kuma wani salon yamutse-yamutse takeyi na ƙularwa ita a dole mai ciki (😂Lulu problems kenan🤣👏).
Abinda Lulun keyi ya matuƙar sosa zuciyar Alh. Sulaiman, dan kasancewarsa gogaggen mutum mai huɗɗa da jama’a a fannoni da dama ciki harda matan banza. Ya fahimci da wani manufa yarinyar ke nuna musu ciki su tabbatar yana nan. Ya cije lips ɗinsa a hankali tare da miƙewa yana kallon Dada. “Zan ɗan je na wani waje na dawo Dada. Kai Tajuddeen ka jirani dan zamuyi magana”.
A tare suka amsa masa da adawo lafiya, yayinda Lulu da ke shan kunun nata na fama ta ɗan laɓe baki hankalinta a television kamar bata san mi suke ciki ba. Har ya fice bata tanka ba kuma, sai a zuciyarta take ayyana (Kuyi duk ku gama ƙulla makircin naku ina biye daku har a gaba danan dan inaji a jikina za’a samu canjin wajen zama in har akwai abinda kuke shirin)…
Alh. Sulaiman na fita asibiti ya nufa wajen Dr Olivia, kusan a tare suka iso da ita cikin asibitin. Koda suka ƙarasa cikin Office cikin tsatstsareta da idanu ya ce, “Ya akai cikin yarinyar can bai fita ba? Bayan na baki duk abinda kika buƙata da ga gareni?”.
Ɗan murmushi baturiyar likitar tayi mai cike da ma’ananoni. Kafin ta ɗago tana kallonsa cikin ido. “Ciki kam na zubar da shi, kuma na saka amata wankin ciki da gwaji domin tabbatar da fitarsa. Sai dai in wani ta sake samu kum…..”
“You are vary stupid Olivia. Kalleni da ƙyau na miki kama da bakar fatar da zaki rainama hankali ko ki kalla wawa?. Niba likita bane, kuma banda ilimin likitanci, dan haka yaya akayi?!! Ciki bai fita ba!!?”.
Yanda yay maganar a tsawace da buga tebirin ya sata ɗan zabura kaɗan. Sai kuma ta watsa masa harara ta koma cikin kujerarta ta lafe. Sosai ransa ya sake ɓaci matuƙa, zuciyarsa sai zallo take da tuƙuƙi a cikin ƙirjinsa. Ya nunata da yatsa da faɗin,……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣4️⃣
…….“Look Olivia, kin san dai zan iya aikata miki komi ko? Ciki harda datse jijiyar numfashinki. Kin sanni na sanki ciki da bai, ki faɗa min yanda akai ciki bai fitaba?”.
“Mi kake so na sanar maka bayan wanda na faɗa?, Na faɗa maka iya abinda na sani ai, kasan irin haɗarin dana saka kaina wajen maka yanda kake so bayan kauce ƙa’idar allurar daya kamata nai mata. Kaifa ka kawo allurar nan kuma na cika umarninka nai mata, a gabanka komai ya faru kuma ko balle kace na yaudare ka”.
“Ƙarya kike Olivia, sai dai idan fakar idona kikai kika canja allurar dana baki. Dan babu macen da aka taɓa gwada wannan allurar a kanta hakan ta kasance kema kin sani. Sannan ƙarya kike bakuyi mata wankin ciki ba”.
Shiru tai kamar bazatace komai ba, sai hucin ɓacin rai takeyi kamar yanda shima yake yi. Wayar landline ta jawo tai kira, kai tsaye ta bada umarnin a sameta a Office. Mintuna baifi uku ba wani nurse baƙin fata ya shigo. Cikin girmamawa yayma Dr Olivia barka da shigowa tare da ɗagama Alh. Sulaiman hannu a taƙaice. Dr Olivia ta dubesa bayan ta zaro wani file a gefenta ta miƙa masa. Amsa yay cikin rashin sanin mizaiyi da shi.
Ta ce, “Buɗe”.
Babu musu ya buɗe tare da ɗan duddubawa, sai kuma ya ɗago yana kallon doctor. Kafin yace wani abu ta tareshi da faɗin, “Ban sakaka yima mai wannan file ɗin wankin ciki ba a ranar data samu miscarriage?”.
Ɗan jimm yay alamar tunani, sai kuma ya dubeta yana cewa, “Ƙwarai anyi haka doctor, sai dai kuma an samu akasi ai a ranar bamuyi mata ba saboda yanayin mahaifarta mukace bayan kwana biyu su dawo sannan ta huta saboda sun matsa a sallameta….”
A zafafe Alh. Sulaiman ya yunƙuro zaiyi magana Dr Olivia ta girgiza masa kanta. Ita ta ƙara fuskantar Nurse ɗin da faɗin, “Amma miyasa baka sanar min ba? Sannan da baki ka faɗa musu ko’a rubuce?”.
Kai tsaye yace, “Nazo sanar miki sai na samu kin fita. A rubuce kuma muka basu gaskiya, kuma ita muka bamawa ma a hannunta ai”.
“Okay zaka iya tafiya”.
Ɗan rissinawar girmamawa yay tare da ajiye mata file ɗin ya fice. Yana rufe ƙofar ya saki murmushin mugunta, a zuciyarsa yace (Ƴan iska ai dama nayi alƙawarin saina kuɓutar da yarinyar nan. Wankin ciki kuma ina kan sani naƙi yinsa bayan nai mata allurar tsaida jini da sauri ta yanda cikin bazai fita ba. Ina Musulmi baƙar fata bazan taɓa bari a cutar da wani musulmi ba in sha ALLAHU in dai ina asibitin nan. Tunda har naji hirarku dama nai alƙawarin taimaka mata dan na fahimci zaku cutar da ita ne bada saninta ba).
A ciki kuwa shiru Office ɗin ya ɗauka. Da ga Alh. Sulaiman har Dr Olivia kowa ya kasa cewa komai. Sai can ta nisa da ƙyar ta katse shirun da faɗin, “Yanzu ka yarda na maka aikinka ko? Sannan babu kuskurena a ciki na turata inda za’a mata wankin ciki, kaga kuma sun basu damar su dawo amma baku dawo ba, hakan na nufin yarinyar bata son rasa cikinne ko wani dalili daban…..”
Cikin wani irin baƙin ciki da zafin zuciya Alh. Sulaiman ya furta, “Dalilinta na banza. Ciki kuma dolene a zubar da shi”.
“Gaskiya bazai yiwu ba, inba haka ba kuwa komai zai iya faruwa kamar yanda na faɗama Mrs Garko. Ciki kuwa harda rasa ranta. Ni kuma bazan iya gangancin aikata haka ba a wannan gaɓar dan zai zama taka doka, cikin wata biyar da kusan sati biyu, taɓashi da niyyar zubarwa ai kowama yasan ganganci ne. Kawai ku barta ta haihu tunda tana son abinta”.
“Ashe zan kashe yarinyar nan kuwa!!” Alh. Sulaiman ya faɗa a wani irin kausashe jikinsa har ƙyarma yakeyi. Ita Dr Olivia ma duk sai tsoro ya kamata. Nurse ɗin nan ne yay knocking ƙofar ya shigo, cikin girmamawa ya aje wani file a gaban Dr Olivia a yanayin dafa tebirinta, hakan ya bashi damar zare ƙaramar wayar da ya ajiye batare da sun lura ba saboda rufewa da idanunsu sukayi. Daga haka yay ficewarsa yana ɗan murmushi….
Fitarsa kusan da mintuna biyar sai ga Alh. Sulaiman ya fito ransa a matuƙar ɓace tamkar zai kifa a cikin sassarfa. Nurse ɗin nan yay murmushi da biyo bayansa da sauri-sauri. Sun ɗan yi nisa a doguwar barandar yaji kamar ana binsa a baya. Jiyowa yay cikin sauri sai sukai arba da Nurse ɗin nan. Kamar zai yi magana sai kuma yay shiru sakamakon tare numfashinsa da Nurse ɗin yay cikin harshen Hausa. Mamaki ne ƙarara ya bayyana a fuskar Alh. Sulaiman, duk da kuwa hakan ba wani abun ai mamakin bane kasancewar matashin saurayin baƙin fata. Amma gaskiya bai tsammanin jin Hausa a bakinsa ba. “Sunana Usman B Sa’eed. Bahaushe haihuwar Nigeria girman Canada. Na biyoka ne nan saboda jin ina son taimakonka matsayin ƙabilata kuma addinina.”
Kamar Alh. Sulaiman zai yaɓa masa magana sai kuma dai ya haɗiye, yaga ya kamata yaji ƙarshen zancen. Usman ya cigaba da faɗin, “Dr Olivia bazata baka haɗin kai ba dama, dan kasan turawan nan da son bin ƙa’idar abu. Sannan gaskiya ta faɗa in har ta aikata sake zubda cikin aka samu matsala to akwai babbar ƙura da ku kanku zata iya shafarku. Karka manta anan sun san hakkin ɗan adam ba irin yankuna mu na Africa bane ba da zaka iya yin komai ba komai. Na fahimci cikin irin wanda mu mutanen Hausawa muke gudune wato na shege shiyyasa kuka matsu ku zubar. Dan haka zan taimaka muku ta yanda zaku salwantar da shi cikin sauƙi batare da kowa ya fahimta ba. Sai dai zai kai haihuwa, amma za’a haifesa ba’a raye ba, dan zan dinga mata allurar da yaron zaita ruɓewa a cikin nata batare da an fargaba itama kanta bazata fahimta ba dan na gane bata so a zubar da shi shiyyasa taƙi dawowa wankin ciki”.
Sosai Daddy yake nazartarsa, amma abin mamaki ya kasa hango yaudara a tattare da shi. Dan Usman irin mutanen nan ne masu maida abu serious ka kasa fahimtar gabansu da bayansu. Kai Daddy ya ɗan jinjina kawai tare da miƙa masa hannu. “Zan iya baka number ka sameni a gida bayan nayi shawara”.
“A babu damuwa ai Alhaji”. Cewar Usman cikin dakewa. A zuciyarsa kam sai dannama Alh. Sulaiman zagi yake kala-kala. Dan yana ayyana sune masu fita ƙasashen waje suna zubar mana da mutunci ana kallonmu wawaye creminal. Ya bashi number wayan suka rabu, da ga haka ya fice a asibiti ya samu taxi ya shiga dan anan baida lasisin tuƙi. Maimakon gida sai ya nufi can wani joint a bayan gari kaɗan, wajene na sheƙe aya matuƙa dan mata na yawo ne babu sutura. A can ya samu ya huta zuciyarsa ta huce da samun damar yin tunani akan Usman Nurse. Ya fahimci wannan ita kaɗaice mafita kam a garesa. Dan yana son tabbas shegen cikin nan ya zube saboda shine sharar fage na farko da yake son ƙuntata rayuwar Smart da ita. Kafin ya tafi matakin farko akan Daddy da Smart ɗin harma da Uncle Yousuf, dan akan Lulu yake son ya musu tarko su ukun ta yadda zasu koma su kansu basu yarda da kansu ba. Wannan shine sabon plan ɗin da ya canja akan kowanne su. Tajuddeen kuwa lokaci yayi da zai kaɗa kansa ya bar Canada. Dan ya gama masa aikin da yake so, dama amfani kawai yake da yaron nasa a matakin dalillai biyu. Na farko manufarsa tun fil azal. Na biyu halin ciwo da yake ciki akan yarinyar shiyyasa yake biye masa kamar gaske dan ya samu kwanciyar hankalinsa. Dan gaskiya yana ƙaunar yaron fiye da sauran ƴaƴansa. Saboda kasancewar sa namiji ɗaya tilo a cikinsu. Yana ganin bayan ya tsigesa mataki na biyu da zaibi a kansa shine bin shawarar amaryarsa akan haɗashi aure da ƙanwarta, dan ya gamsu da bayanin datai masa ya kuma ɗauki shawararta. Sannan ita kanta Dada lokacin gama nata aikin yayi.
Koda ya koma gidan sai bai cewa Dada komai ba koda ta tambayesa ya batun zuwa asibiti. Sai da ta ƙara maimaita masane ya ce ta saurareshi yana nazari ne. Badan Dada taso ba dole tai shiru ganin ya haɗe fuska. Ummita dake laɓe tana jinsu, sai dai bata so jin Alh. Sulaiman yay shiru ba. A lokacin da duk wannan cakwakiya ke faruwa Smart na can cikin farin cikin samun nasarar cin ƙwallon da sukai tsakaninsu da abokan hamayyarsu ƴan Model Unitet a wannan ranar……
Bayan kwanaki biyu Alh. Sulaiman ya kammala yanke hukunci akan zancen Usman Nurse, sai dai bai nemesa ba sai da ya saka akai masa bincike a kansa tsaf. Inda aka kawo masa bayanai akan tabbatar da cewar karatu ne ya kawo mahaifinsa ƙasar Canada, amma asalinsu ƴan Nigeria ne. Anan Usman ya girma dan yana da shekara kusan goma iyayen nasa suka dawo Canada, sai dai fa yana yawan zuwa ƙasar haihuwar tasa. Usman dai a zahirance baya jin magana sam, dan duk wani ɗani’u na turawan nan yana zubasu musamman neman mata, kuma kamar yanda yake a turai hakan ba komai ba suma iyayensa basu ɗauke sa komai ba. Bai taɓa aure ba amma yanada ilimi mai dan babban Nurse ne shi ɗin. Wannan bayanai sun ƙawatar da Alh. Sulaiman, dan ya nazarcesu tsaf da fahimtar su a yanda makauniyar zuciyarsa ta tabbatar masa. Abinda bai sani ba Usman yarone mai matsanancin kishin ƙasarsa da ma yankinsa na Africa har ma da addininsa duk da waɗan nan rashin jin nashi. Wannan aƙidar tasa tasa ko kullum yake cikin yawo tsakanin Nigeria Da Canada kamar wani ɗan sama jannati. Dan ko aikin ma anan da ƙyar mahaifiyarsa ta samu ya yarda yakeyi, amma duk da haka sai da yaje ainahin ƙauyensu ya buɗe wani ƙwarya-ƙwaryan asibiti ya zuba likitoci da ke aiki a cikin kuɗi ƙalilan wa marasa lafiya. Koda Alh. Sulaiman ya gama tattare abinda yake buƙata sai yay ma Dada wayo akan ta koma wajen Baba, ciki Lulu kuwa su barshi ta haifi abinta kawai tunda dai Dr Olivia ta tabbatar musu akwai matsala. Ba haka Dada taso ba, sai dai bata iyayima ɗan nata musu, ganin kuma ya dawo da passport ɗin Lulun da Ummita ya basu ya sakata jin kwanciyar hankali, dan haka badan taso ba ta shirya ta koma wajen mijinta da al’amarin nata ya sashi fara tsarguwa shima. Sai dai baice mata komai ba tunda ta ce masa wasu kaya zata duba a Canada ɗin dama kafin ta wuce……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣5️⃣
……Ko kaɗan Lulu bata nuna damuwa da tafiyar ta Dada ba duk da kuwa a ƙasan zuciyarta cinkushe yake matuƙa, amma plan ɗinsu ita da Ummita ya sakata dakewa abinta ta nuna komai ba komai har Dada ta wuce. Washe gari shima Tajuddeen mahaifin nasa ya janye ra’ayinsa ta hanyar tura sa Nigeria da saƙo. Ko kaɗan Tajuddeen bai kawo komai a ransa ba ganin shima Alh. Sulaiman ɗin yayi shiri wai zai wuce ƙasar Brazil ne yin wani business, sai dai ɗan nasa na wucewa yayo sau da baya. Sabon gurin daya shirya za’a kai masa su Lulu acan wani ƙauye ko yanki za’a kirashi ma ne oho ya wuce. Wajene tsibiri ne, dan a tsakkiyar wani irin makeken ruwa mara iyakar kallo tsibirin yake. Gidajene kawai na masu zuwa hutawa a wajen da yawon buɗe ido, sai jiragen ruwa ne kawai ke iya kaika cikin tsibirin. Wajen kam a kwai daɗin zama musamman ga wanda suka je hutawa, zaka tabbatar da hakanne ne idan kaga yanda mutane ke nishaɗi musamman ma masoya da masu kuɗi……
Kamar kullum yau ma bata fito ba har sai da Ummita ta kamma kimtsa gidan, yay tsaf abinsa sai tashin ƙamshi da ɗumi mai ratsa ɓargon jiki daya gauraye ko’ina. Wando da riga ne a jikinta marasa nauyi, dan haka matashi cikinta ya samu damar fitowa ɗas da shi. Yau gaba ɗaya kasala takeji, dan da ƙyar ta iya fitowa dan yunwa data addaba mata ya sata fitowa ta samu abinda zata ɗan ci. Kai tsaye kitchen ta nufa inda Ummita keta ɓuruntun dama mata kununta, koda tai sallama kafin ma Ummita ta kai ƙarshen amsawa ita harta isa ga freight, ruwa ta ciro mara sanyi ta sha, tana ajiye bottle ɗin da sauran wanda ya rage ta nufi Ummita. Fuskarta da murmushi take faɗin, “Har yanzu ƙarnin kifin nan da Dada tasa kika dafa mata a gidan nan ya ƙi fita wlhy Ummita”.
Da mamaki Ummita ta ce, “Kai aunty dan dai baki so ne kawai, amma wlhy ni banjin komai sai ƙamshin fresheners a gidan nan.”
Cikin ɗan yamutsa fuska da tsaki ta ce, “Wlhy Ummita yanzu ne dai bana so, amma da ai kafin na ci miki nama naci kifi, sai dai yanzu na rasa miya haɗani da shi haka ko ƙamshinsa bana so”. Da dariya Ummita ta ce, “Aikin Unborn ne ai Aunty”. Shiru Lulu tai tana kallonta kamar mai nazari kosan tuna abu, abinda ke ƙoƙarin tuna kam nasa ne a zuciyarta ya zo mata. Tabbas Aliyu bama yancin kifi kwata-kwata idan bata manta ba. A take ta haɗe fuska kamar a ɗan ƙufule ta ce, “Ni shikenan saboda wannan cikin duk abinda baya ci nima na daina ci koda ina sonshi, sannan abinda yake so dole sai na so shi kamar abin asiri?”.
“Wakenan Aunty?”.
Cewar Ummita cikin nuna mamakin furucin uwar ɗakin nata. Sai dai maimakon bata amsa sai taga ta juya tama fice a falon tana ɗan dafe kai. Bata kawo komai a ran nata ba game da dafe kan ta cigaba da zuba mata kunun gyaɗar a flaks ɗin da ake zubawa. Ta kammala idonta ya sauka akan sauran ruwan da Lulu tasha ta ajiye, ta san da wahala ta sake shansa. Dan haka ta ɗauka ta shanye ta jefa bottle ɗin a shara sannan ta ɗauki flaks ɗin da ƙaramin kofi tabi bayan Lulu. Ɗan turus tai na mamakin ganinta baje a kujera tana barci kamar ba yanzu ta baro ta a kitchen ba. Sai tai dariya da jin tausayin ta. Ta ajiye flaks ɗin itama da nufin komawa kitchen ta gyara kayan datai amfani da su a aikin itama kanta ya sara, da sauri ta dafeshi tana mai ambatar sunan ALLAH, jin hajijiya na neman yadda ta a ƙasa da bin bango ta fito falon itama, sai dai kafin ma ta kai ga kujera ta zube ƙasa, daga haka bata sake sanin ina hankalinta yake ba itama….
Duk abinda ke faruwa Alh. Sulaiman na kallo ta camera da ya saka musu kamar yanda Ummita ta zarga dama, wata shegiyar dariyar basanci ya saki sai kuma ya gimtse fuska duk a lokaci guda. Wayarsa ya jawo a gefensa tare da shaƙar cocaine ya wani girgiza kan nasa da wani irin style na ƙwararrun ƴan cocaine sannan ya kai wayar kunnensa. Cike da izza ya furta “Nan da awa ɗaya ku tabbatar su da duk tarkacensu suna a gabana” da ga haka ya yanke kiran batare da jiran an bashi amsa ba da ga can…
Matuƙa hankalin Lulu da Ummita ya tashi a lokacin da suka farka da ga nannauyan barcin da ya samesu suka ga kansu a inda ba’a nan suka kwanta ba. Cikin matsanancin firgici suke kallon juna kafin su miƙe duk a zabure su fara dube-duben inda suke ɗin. Falo ne madaidaici sai dai akwai komai a cikinsa sai bedrooms guda ɗaya mai ɗauke da gado biyu, sai kitchen. Ko ina a kulle yake ta hanyoyin waje sai dai suna iya hango makeken ruwan daya zagaye ko’ina da ina ta cikin gilashi. Basu iya ganin mutanen da ke kai kawo balle iya jiyo hayaniya saboda gilashin manne da ginin bullet proof ne. Yunwar da Lulu keji dan a yanzu sam bata da jimirinta ya sata fara jin yuuu-yuuu kamar jiri zai yadda ta. Da sauri takai zaune cikin rawar murya tace, “Ummita yunwa”. Hankalin Ummita ya tashi matuƙa dan haka ta miƙe cikin rawar jiki ta fara dube-duben ko zata ga abinci, cikin aminci ALLAH ta ganshi an ajiye a gefe kan ƙaramin dining table mai kujera biyu. Ɗakko mata tayi, jikin Lulu har rawa yake wajen karɓar abincin ta fara turawa, duk da baya mata daɗi haka takeci ko zata samu nutsuwa. Tan kammalawa ta fara sheƙa amai kamar zata fidda har hanjin cikinta. Ta jigatu matuƙa dan Ummita har da kukan ta, ita ta taimaka mata ta gyara jikinta ta canja kaya ta hau gado ta kwanta ta dunƙule a waje ɗaya cikin rawar sanyi, kafin wani lokaci zazzaɓi mai zafi ya rufeta. Kuka sosai Ummita ta zauna ta dingayi, babban tashin hankalinta shine basu san wanene ya kawosu nan ba kuma. Duk da suna zargin Alh. Sulaiman sai dai zukatansu sun kasa zama waje guda. Sosai Lulu bata da lafiya gaba ɗaya a wannan daren, gasu a rufe balle Ummita ta fita ta nemo musu taimako. Sai da barcin wahala ya ɗauke Lulun ne Ummita ta samu damar tashi zuwa kitchen ta shiga bincike, ta ɗan samu nutsuwa ganin kayan abinci harda kayan tea, sai dai babu gyaɗa, ga shi a yanzu komai Lulu baci take ba da daɗin rai sai wannan kunun….
Kwanakin Lulu kusan uku tana fama da zazzaɓi kafin ALLAH ya bata lafiya ta dawo dai-dai, duk ta rame sai wani uban haske data ƙara. Kamar ance su dawo nan ciki ya fara girma, ga shi bata samun kunun gyaɗar da take so sai ɗan tea da take sha kaɗan-kaɗan, abincin ma Ummita kan zauna taita lallaɓata har sai taci ko yaya ne, duk da data gama take yin amansa. Wani bai taɓa zuwa musu ba, sai a randa suke cika sati guda ne suka wayi gari suka ga an ajiye musu kayayyakin abinci dana buƙata a falo, ciki harda gyaɗa abin mamaki. Kallon-kallo kawai sukeyi, a ransu sunajin tabbacin duk abinda sukeyi kenan ana sane da su. Murmushi Lulu ta saki a karo na farko, dan dama kawo su nan ya tabbatar mata da hasashenta akan kawun nata kenan. Basu da hurumin cewa bazasuci abinda aka kawo musun ba, sai dai Ummita kan zauna ta tofeshi da addu’oi sannan. Wannan abin da take ɗin ne ya sake sakama Lulu nutsuwa da ita. A hankali shaƙuwa ta cigaba da shiga tsakanin Ummita da Lulu, har takai yanzu Ummita na ɗorama Lulu karatun Alkur’ani da na wasu littattafan addini da take da su kamar yanda Lulun ta buƙata. Sannan cikin dare Ummita kan tashi tai nafilfilinta, tun Lulu najin damuwa da takurar hanata barci da Ummita keyi kasancewar bata saba da zama mutum biyu a ɗaki ɗaya ba har itama ta fara tashi tana sallar. Hakan ya saka Ummita a farin ciki sosai, haka itama Lulun wannan yanayin na sata jin farin ciki da jinta kamar wata sabuwar hallita, dan wata sabuwar nutduwa ce ta sake zo mata. Kullum sai Ummita ta mata addu’a ta bata a ruwa ta sha, sannan takan gaya mata wasu akan ta dingayi tana shafe cikinta da shi. A haka suka cika wata ɗaya a wannan juyayyen waje da basu san inane ba, sai dai hakan bai hana Lulu cigaba da tattara bayanai akan kawun nata ba, ranar da suka cika wata guda sai ga baƙonsu na farko daya fara ziyararsu. Wato Nurse Usman, babu wanda ya ganesa a cikin su Lulu, shi kuma bai nuna musu sani ba ya ce kawai yazo duba lafiyarta. Da taƙi sai yay kiran Alh. Sulaiman. Wannan ce ranar ta farko da su Lulu suka fahimci wanda ya kawo su nan ɗin duk da ita dama Lulu ta gama bama zuciyarta shi ɗinne. Al’amarin ya sake dilmiya Lulu a kogin mamaki game da abinda kawun nata ke yi akanta, sai dai batace komai ba ba kuma ta hana Nurse Usman ɗin yin aikinsa ba duk da tana ɗar-ɗar tana son a na duba mata lafiyar jaririnta kuma, shot note da Usman ya ajiye mata ya sakata sakin ajiyar zuciya. Shima sai yay mata ɗan guntun murmushi. Ya dubata tare da bata magunguna bayan ya tabbatar mata da lafiyar cikin nata. Tai masa godiya ya tafi. Sunyi mamakin ganin bayan ya kammala sai da ya kira akazo aka buɗe masa ƙofar sannan ya fita, hakan na nufin akwai wani a waje da ke gadinsu kenan ma kamar acan inda suka baro. Ganin Ummita zata saka damuwa a ranta Lulu tai mata murmushin kwantar da hankali. Note ɗin Usman ta miƙa mata, sai ga Ummita na murmushi da sauke ajiyar zuwa. Lulu ta lumshe idanunta a hankali ta furta “Yanzu kin fahimci wasan namu ne ko? Karma ki tadama kanki hankali yanzu lokacin tattara bayanai ne, dan haka babu buƙatar cigaba da shiga damuwa kuma farin ciki kawai domin kama tsuntsu mai wayo”.
Ƙaramar dariya Ummita tayi, yayinda a ƙasan zuciyarta tamaji ta fara tsoron Lulu, dan fa ta fahimci atsabibiyar kanta ce ashe…..
Tun daga wannan ranar Lulu da Ummita suka sake sakin jikinsu tamkar basu da wata damuwa, ga ciki nata haɓaka da bunƙasa cikin ƙoshin lafiya. Ganin yanda suka sake jiki da walwala ya saka Alh. Sulaiman bada umarnin a ɗan dinga buɗe su, sai dai yana son duk inda suka saka ƙafa a tsibirin nan yana sani. Dan ya zagayesu da mutanensa kusan goma batare da sun sani ba. A cewarsa yanzu plan zai fara. Kamar yanda itama Lulu take ji a ranta yanzu wasan zai fara……..✍️
_🤣🤣Hahaha anayi muna cin gyaɗa mai gishiri🥱🥱🚴_
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣6️⃣
…….Tun a randa suka fara fitowa Lulu ta fahimci zagaye suke da idon yaran Alh. Sulaiman, amma maimakon ta razana sai ma tayi murmushi. Batace da tacema Ummita komai ba akan hakan, sai ma zunguran Ummita data shigayi game da sanin wacece ita? Da yanda akayi ta yarda ta biyosu Canada. Tuni hawaye suka cika idon Ummita. Bata hanasu zuba ba sannan bata sharesu ba, sai da ta jiƙe gaban rigarta sosai kafin cikin shashshekar kuka ta ce, “Sunana na yanka Fatima. Naci sunan kakata ne shiyyasa ake kirana Ummita. Asalinmu ƴan wani garine ɓagwai a ƙauyen bichi. Anan nai karatun primary ɗina, da ga baya aka kaini boarding school a wata makaranta da ake kira GGASS Ɗan/zabuwa. Naje har js 3 aka cireni na koma cikin garin Kano hannun yayata da ke aure acan sakamakon rashin lafiya data kwanta. Jeka ka dawo na koma zuwa ina kula da yayata a gidan mijinta tsahon shekara biyu harta fara samun lafiya. Tun ban wuce shekara ɗaya a gidan ba mijin yayata ke nunamin wasu abubuwan rashin ɗa’a, sai dai bana kulashi sai da naga abin na neman wuce gona da iri na nuna inason komawa gida dan ban son faɗama yayata na tayar mata da hankali. Amma sai iyayenmu sukaƙi yarda yayar tawa ma harda kukanta, acewarta idan na tafi wazai ringa kulawa da ita da ƴaƴanta biyu kamar ni. Tausayinta ya kamani sosai, dan haka na haƙura na zauna, sai dai na ɗauki matakan kare kaina tako ina har takai mijin nata shima ya daina shiga sabgata ya kama kansa. Ashe lumbu-lumbu yay min, dan sai da ya bari na shagala sannan a wani dare ina gab da kammala ss3 ya bankama yayar tawa maganin barci ya keta mun mutuncina. Maganin daya banka mata yay sanadin barinta duniya, na shiga tashin hankali irin wanda baida misali, sai dai na gagara faɗama kowa asalin al’amarin har akai sadakan uku. Ina murna zan koma gida sai babana yace na zauna tare da gwaggonmu mu kula da yaran harna ƙarasa jarabawar neco da waec da zamu fara. Naso tada hankalina amma akaita tausata, ganin akwai gwaggonmu ya sani jin zan daure ɗin. Mun fara jarabawa ina a cikin yanayin rashin jin daɗin jikina. Haka dai naita daurewa yayinda iyayenmu a bayan fage batare da sanina ba suke shirye-shiryen aurar da ni wa mijin yayata matsayin madadi waina riƙe yaranta. Da farko ya yarda sai dai a randa muka gama jarabawar ƙarshe na kaita a wahalce, tun daga makaranta aka wuce dani asibiti, inda a gwajin farko aka sanarma gwaggona da tazo inada shigar cikin wata biyu. Tashin hankali kenan wanda ba’a saka masa rana, babu bin ba’asi babana ya hau dukana Sakamakon zugar da mijin yayata yay masa akan dama ance ina yawon banza ai, baya son ya faɗa ne ace dan karya auranne yake son zamewa. Iya jijjiga kamalamansa sun jijjigani, yayinda ɓacin rai ya saka baba rantsewa bazan zauna masa a gida ba. Hankalin mahaifiyata ya tashi, amma sanin halin mahaifinmu ya hanata cewa komai, sai shawarar turani Abuja data yanke wajen ƙaninta. Matar ƙanin mamana na samu damar warwarewa komai da ya faru, ranta ya ɓaci matuƙa ita da ƙanin mamana, dan haka suka ɗaukeni muka juya Kano suka shigar da ƙara kotu tare da neman lawyer daya san aikinsa sai aka haɗamu da ke. A lokacin baki jima da dawowa Nigeria ba kamar yanda naji ance, dan hausanki ma ba wani sosai yake fita ba. Kin taka rawar gani a rayuwata ta hanyar tabbatarma mijin yayana MACE MUTUM ce (Rahma Abdull-majeed. Wanda bai karanta littafin nan ba wlhy anyi bashi🥱). Dan sai da kika turashi gidan yari har yanzu kuma yana can. Uncle ɗina bai saurari iyayena ba da suka shiga nadama sosai ya ɗakkoni muka sake dawowa Abuja. Inda ya nema min makaranta na fara. Ga rainon ciki inayi, cikin danai matuƙar tsana a rayuwata har ALLAH ya kaini ranar haihuwa. Sai dai alhmdllh jariri baizo da rai ba. Hakanne ya sani farin ciki na maida hankali a karatuna. Bana zuwa gida saboda gudun zunɗen mutanen ƙauye harna kammala karatu na na samu result mai ƙyau, ina cikin neman aiki ne sai ga Hajiya Shuwa a gidan mu kasancewar tana huɗɗa da aunty na, tana kawo mata turaren wuta. Jin ina neman aikin taimin tayin wannan aikin, sai dai tace aikin na shekara ɗaya ne kacal shiyyasa kawuna ya amince da sauri, ni dai bance komai ba dan banjin zanje ɗin, sai a randa na ganki matsayin wadda za’aima aikinne ya sani yarda da sauri-sauri domin rama alkairi da kikai min nima….”
Tuni hawaye sun jiƙe fuskar Lulu, jik 10inta har wani tsuma yake kamar wadda ake kaɗama gangi. Lura da hakan ne yasa Ummita kamata suka koma ciki batare da ma lokacin da aka basun ya cika ba…..
_________★
A ɓangaren Dada tun a washe garin da Alh. Sulaiman yasa aka canjama su Lulu wajen zama yay kiranta cikin tashin hankali da makirci yake sanar mata baiga su Lulu ba, yazo gida ya samu sun gudu. Yasa ƴan sanda nemansu da ga baya suka fahimci sun bar ƙasar ne da taimakon wani dan har note aka bar masa. Hankalin Dada yay masifar tashi har takai ta kasa controlling kanta Baba Garko ya fahimta. Tambaya ya shiga jera mata wadda ta kaita da gaya masa cewar Lulu ta gudu da ga Canada, kuma suna zargin wani ne ya sace ta. Cikin matuƙar mamaki Baba Garko ya ce, “Canada kuma Hajarah, miya kai Mawaddat Canada ko ita da mijin nata ne?”. Wannan kalma ta Baba ce ta dawo da Dada a hayyacinta. Duk kuma sai ta daburce ta rasa abin cewa har takai Baba Garko ya daka mata tsawa, tasan halinsa baya ɗaukar raini, idan ya juye mata takan rasa gane kansa, kafin yay hakanne akan jima shiyyasa take samun damar iskancinta. Waya ya ɗauka ganin bazata bashi gamsashiyar amsar da yake buƙata ba yay kiran Daddy. Sai dai wayarsa taƙi shiga, yasan hakan nada nasaba ne da yanayin network. Ganin zancen waya ma bazai bashi yanda yake buƙata ba a ranar ya saka autansa namiji da tunda yazo da iyalinsa bai koma Saudiyya inda yake aiki ba ya yanka musu ticket, dan yace yau bazai sake kwana a ko’ina ba sai a Nigeria, saboda ya fahim al’amarin babba ne. Hankalin Dada ya sake tashi, amma tasan a wannan gaɓar bata isa yi masa wani daɗin baki ya dakata ba, dole ta shirya suka wuce a tare.
Sunma Nigeria ƙasar haihuwarsu saukar dare, hakan sai ya sirranta dawowar tasu suka samu damar isa gida cikin kwanciyar hankali. Kowa ka gani a gidan Baba Garko ma’aikata cikin farin ciki yake da samun lafiyar tsohon abin son kowa. Mai tausayi da son ƙyautata rayuwar na ƙasa da shi, mai jan ɗan aiki jikinsa tamkar ɗan uwa ba bawa ba. Bayan albashinsu da ba’a taɓa tauyewa ba a koda yaushe cikin musu alkairin yake. Ko Zakka ya fitar sukan samu kaso mafi tsoka duk da Dada bata son hakan. Sannan duk abinda ya samu iyalansu ko lafiyar jikinsu yakance su sanar masa dan shine da hakkin wannan. Wannan yasa su jin ƙaunarshi da shiga a tashin hankali a duk lokacin da suka ga yana a cikin damuwa ko farin ciki. Sam hankalin Dada baya a jikinta, suna isowa sashenta ta wuce, layinta na Nigeria ta ɗora a waya sai dai kafin ya gama dai-daita duk ta ƙosa, hakan ya sata amsar wayar mai aikinta domin kiran Daddy. Amma abin mamaki sai ta samu number busy, bata kawo a ranta da mijinta Daddy ɗin ke kiran ba, dan haka ta cigaba da jera masa kira. Shiko Daddy dake waya da Baba Garko ganin baƙuwar lamba ce yasa koda ya kammala bai ɗaga ba, ganin ma za’a damesa ya sashi saka wayar a airplane mode kawai. Haukane kawai Dada batayi ba a wannan dare jin daga baya ma ta daina samun Daddy ɗin. Karo na farko da taji takaicin rashin riƙe number kowa na jikinsa da ga shi sai Lulu. Dan ko Yousuf ita bata da lambarsa. Matarsa kuwa (Mommy) dama ba huɗɗa take da su ba. Barcin kirki dai Dada bata sameshi a wannan daren ba sam. Tana sallame sallar asuba sai kuma ta fara jerama Daddy kira, sai dai har lokacin wayar bata shiga. Gaba ɗaya ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta kuma kasa zuwa inda Baba Garko yake. Dan gani take kamar yana riga ya gama jin komai da komai. Tayi kiran Sulaiman kuma shima wayarsa bata shiga ba sam…
A ɓangaren Baba Garko ya gama fahimtar akwai matsala, sannan koma minene akwai saka hannun matar tasa a ciki. Yay kiran Daddy kuma dan yaji gaskiyar zance game da zuwan Lulu Canada sai ya samu numbersa busy. Akan Uncle Yousuf ya maida akalar kiran nashi, inda yaji komai da komai, yana gama wayar da Uncle Yousuf ɗin ne kuma kiran Daddy ya shigo masa. Maimakon ya tambayesa kamar yanda ya tambayi Uncle Yousuf sai ya canja kawai suka gaisa ya sanar masa yazo Nigeria, yana son da safe ya samesa a gida da wuri. Daddy yayi farin cikin jin Baba ya samu lafiya, sai dai ya shiga mamakin jin kiran gaggawa da yake masa. Wanda yasan koda bai kirashi ba tunda yaji ya dawo ƙasar da safen dole zaije gidan duba shi.
Zuwa ƙarfe bakwai da rabi duk wanda Baba Garko ya buƙaci gani a gidan nasa ya iso. Dan harda ƴaƴansu ƙannen Alh. Sulaiman ɗin. Uncle Khamil da auta da suke kira Uncle Sadiq ne kawai babu dan shi sun barosa acan, sai kuma Alh. Sulaiman da shima dai fushin da Baba keyi da shi yasa bai saka shi a cikin meeting ɗin gaggawar ba. Sosai kowa ke cikin farin ciki da ganin yanda mahaifin nasu ya samu lafiya kamar bashi ba. Zamansu babu jimawa ƴan sandan dake bincike akan case ɗin sa suka iso gidan. Ya ce suyi haƙuri suje zuwa anjima zai nemesu yanzu yanada muhimmin uziri ne da iyalansa…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣7️⃣
……..Bayan anyi gaishe-gaishe da taya juna murnar samun lafiyar Baban kai tsaye ya jehoma Uncle Yousuf tambaya kamar jiya. Uncle Yousuf da tunda suka shigo bai kalli inda Daddy yake ba, ko gaisuwa sama-sama yay masa kansa tsaye ya fayyace komai kamar yanda ya faɗama Baba Garkon a dare jiya. Jikin Dada tuni ya jiƙe da zufa, amma tsabar makirci sai ta fashe da kuka wai Uncle Yousuf ɗin ya haɗa mata harda sheri dan ya baƙantata kawai. Ita koda ta ɗakko Lulu dan bata da lafiya ne ta ɗakkota…..” tsawa Baba Garko ya daka mata da cewar, “Yima mutane shiru mutuniyar banza da kullum bata sanin ta girma a rayuwarta. Bance miki ki fita cikin al’amarin auren yaran nan ba tun farko? Rashin lafiya shi mijin nata ne yay dake bazai iya kula da ita ba? Ko kin fishi sanin abinda ya dace yayi akan iyalinsa?!.”.
“Ka gaya min. Kuma ni naga shi ba wani kuɗin da zai iya kulane da ita ga resa ba”.
“Mtsoww zancen banza kenan. To raini ne da son tozarta ni da nunama duniya ban isa ba ya saki zuwa ki ɗakko yarinya a ɗakin mijinta har ki kaita wata ƙasa?”.
“Bafa haka bane sam Alhaji ka fahimceni, yarinyarfa da bakinta ta fayyace min gaskiyar manufar auren …….” nanta ta kwashe komai da komai da Lulu ta sanar mata ta faɗa musu. Karo na farko Uncle Yousuf yay murmushi, yayinda Uncle Muneer ɗanta dake bima Alh. Sulaiman cikin son danne ɓacin ransa da taushin murya kamar yanda ya saba girmamata matsayin mahaifiya ya ce, “Amma Dada duk da a ta gaya miki haka a matsayinmu na wanda muka fita hankali nazata zamu taimaka mata ne ta hanyar kwantar mata da hankali ta haƙura ta zauna a ɗakin mijinta dan yaron nan mutumin kirki ne da duk wasu iyaye na ƙwarai zasu so haɗa zuri’a da shi”.
Harara Dada ta ɓalla masa, yayinda Baba garko ya amshe da “A’a ina zatayi haka ga matar ƙaruna ƴar ƙaruna kuma da hankali bai gama game mata jini ba, ai Mawaddat ɗin ma ta fiki hankali. Wai Hajarah mi kika ɗauki rayuwa ne? Mi kika ɗauki dukiya ne? A zatonki dan ALLAH ya yomu a haka mun zama mafifitane a cikin mutane har a wajensa? Kamar yanda talauci yake jarabawa itama dukiyar da kike gani jarabawace. A wani fanin ma babbar fitina ce ga bawa. Shekara nawa ya rage miki a wannan duniyar da har kike jin wai dukiya har zata cigaba da zame miki abin tinƙaho. Ba tonon silili ba naga ai kema ɗiyar talakawance amma na aure ki, ƙarewa ma mahaifinki masinja yake ga mahaifina mutuncinsa da sanin Yakamata yasa mahaifina cewa na auri ƴarsa. Ban yi musu ba kuma na aureki nake zaune da ke har tsawon shekarun nan matsayin ke kaɗai matata Ashe albasa batai halin ruwa ba….”
Sosai Dada ta daburce dajin kalaman mijin nata irin wanda koda kwatance bai taɓa yinsu gareta ba tun aurensu. Su kansu yaran sai da sukaji shock su dukansu. Dan basu taɓa sanin wannan tarihin ba kasancewar a sanin da sukaima mahaifin mahaifiyar tasu hannunsa a jiƙe yake, sosai Baba kema Dada cin mutunci da ya sakata kuka rurus, agaban ƴaƴan nata ya kuma turketa saita gaya masa inda suka kai Lulu koya bata mamaki da hukuncin da bata taɓa zato ba. Ganinfa ruwa ya ƙarema ɗan kada dole Dada ta fayyace komai game da kai Lulu Canada ita da Alh. Sulaiman harma da yunƙurin zubar mata da ciki da sukayi amma bai fitaba sai da ga bayan nan kuma suka gane hakan, sai kuma kiran da Sulaiman yay mata a jiya cewar ya nema su Lulu ya rasa wai wani ya sacesu, amma yasa ƴan sanda na bincike. A yau da safe kuma yake turo mata text message akan yana zargin Yousuf ne da Smart. Da matuƙar mamaki Uncle Yousuf ke kallonta cikin nuna kansa ya ce, “Ni Yousuf ɗin ko wa?”.
“Inba kaiba waye Yousuf anan, munafuki algungumi. Ai dama kana biye damu tunda muka ɗauke ta kai da shegen yaron nan mara kunya dan bakinku ɗaya ne dama. Dan haka saiku fito da ita tunda ankai ga yanda kake so”.
Tuni fa falo ya hargitse, dan sai kawuna kuma suka nema rabuwa. Yayinda Daddy da tunda ya shigo falon baice komai ba ya zuba musu ido kawai. Hakama Baba Garko. Cikin ɓacin ran yin shirun Daddy Uncle Yousuf ya tashi ya fice a falon dan zuciyar ƴan maza ta motsa da gaske a yau. Ganin bazasuyi shiru ba Baba Garko ya katse hayaniyar tasu da faɗin, “Hajarah kije na sakeki saki biyu, kuma ki barmin gidana a yau har sai kun maido Mawaddat idan da yiwuwar ki dawo sai ki dawo”.
Waɗan nan kalmomi masu dukan zukata na Baba Garko ne suka saka falon yin tsitt, yayinda ya miƙe abinda ya shige cikin bedroom ko waiwayen su bai yi ba. Dada kam da taji kanta na juya mata sai ganinta kawai sukai a ƙasa babu numfashi. Cikin tashin hankali sukai kanta. Duk hayaniyar da ake Baba na jinsu amma har suka kwasheta zuwa asibiti bai ki leƙo ba.
Wannan shine sanadin kwanciya Dada a asibiti na tsawon sati biyu tana jiyya, dan hawan jininta ne yay masifar motsawa. Koda ta samu sauƙi kuma Baba yace duk wanda ya kawo masa ita gida a cikin ƴaƴan nasa wlhy sai ya kwashe masa albarka. Duk kuma wanda yazo yay masa maganarta a gidan nan ma sai ya kwashe masa albarka. Wannan ya saka yaran tsorata matuƙa dan sun san wanene mahaifin nasu akan zuciya, balle yanzu ya sake birkice musu irin yanda basu taɓa gani ba. Gashi sunata kiran Alh. Sulaiman dake matsayin babba garesu kuma silar wannan tashin hankali amma sam sun gagara samunsa. Dole dai aka wuce da Dada gidan Uncle Muneer aka gyara mata sashen baƙi….
*_CANADA_*
Labarin Ummita da Lulu taji ya ƙara musu shaƙuwa matuƙa, yayinda Lulu ta fara tunanin buɗe ƙungiya domin taimakon yara marasa zuwa makaranta dan al’amarin yaron nan data taɓa amsar Number a wajensa bisa titi har yanzu yana ranta bata manta ba, tana jin babu daɗi kuma da bata sami ziyartarsa ba. Ƙungiyar zata riƙe abubuwa uku ne. Karatun yara da rashin galihu ya hanasu yi, sai harkar fyaɗe da kuma shaye-shaye. Ɗari bisa ɗari Ummita ta bama Lulu goyen baya game da wannan ƙyaƙyƙyawan ƙudiri nata. Dan haka suka hau tsare-tsaren su kamar waɗanda akacema gobe zasu bar wannan wajen. Lulu ta cigaba da rainon ciki yayinda Usman ke zuwa dubata da bata magungunan ƙarin lafiya ita da abinda ke cikinta. Alh. Sulaiman kuwa na tunanin allurar gubar da zata ruɓar da tayin cikin Usman ke mata. Akwai fahimtar juna sosai a tsakanin su Lulu da Usman, dan shi ke kawo musu duk wasu bayanai akan Alh. Sulaiman, sai dai a rubuce yake basu, a zahiri kam babu wata alamar dake nuna ko kallon arziƙi sunaima junansu. A haka a haka dai har ALLAH ya kai cikin Lulu haihuwa. Inda ta koma zama da ƙyar tashi da ƙyar. Gaba ɗaya ta canja kamanni saboda kumburin da taɗan yi, dan ma Ummita baiwar ALLAH tsaye take a kanta yanda ya kamata, bata gajiya da yima Lulu da abinda ke cikinta addu’a. Ga Usman na iya bakin ƙoƙarin sa akan komai nasu ciki harda fara shirya musu hanyar guduwa daga tsibirin. Lulu bata taɓa kiran lambar kowa ba tun sanda ta gwada Alh. Sulaiman ya ɗaga. Tunda aka kawosu gidan bai zo ba ko sau ɗaya, hakan ya sasu fahimtar kodai duk cikin takune ko kuma baya ƙasar ne…..
*_UK (LONDON)_*
A ɓangaren Smart wasannin link sun cigaba da tafiya cike da nasarori harma da ƙalubale, inda ALLAH ya ɗaga darajar team ɗin su suka ƙare da maki tamanin da shida, Smart ya jefa ƙwallaye ashirin da bakwai. Hakan ya sashi zama best player na wannan kakar wasa ta bana a ƙasar England, inda ya samu ƙyautar takalmin zinare, team ɗin su kuma ya samu damar shiga babbar gasar premier link na england. A randa su Smart sukai wasan ƙarshe ne ya kasance dai-dai da randa Lulu ta wayi gari da naƙuda. Hankali tashe Ummita tai kiran layin Alh. Sulaiman, amma sai ya amsa mata a daƙile cikin halin ko’in kula. Sai da yaga Lulu na neman rasa ranta sannan yay kiran Usman akan yazo ya dubata, a kallo ɗaya Usman da yay mata ya tabbatar da Alh. Sulaiman cewar dole fa akai Lulu asibiti, dan theatre ya kamata ai mata tilas. Da farko Alhaji Sulaiman ya ɗauki abun babu wasa, sai da fuskanci zai iya rasa damarsa sannan ya amince aka a wuce da Lulu asibiti can cikin gari dan shi tunaninsa mutuwar ɗan a ciki ta jawo hakan. Dai-dai ana shiga da Lulu ɗakin theatre Smart da gabansa keta faduwa ya zira ƙwallo a minti ɗayan ƙarshe da ya rage a tashi wasan. A take garin ya ɗauki ihu, yayinda ya kai ƙasa yay sujida hawayen farin ciki na ziraro masa. Gaba ɗaya teammate ɗinsa sukazo kansa aka rungume juna, suna mai ɗunbin farin cikin shiga a jerin manyan team na duniya da zasu buga primier link kenan, abinda ko’a mafarki ba’a taba kawo musu ba. Amma Alhamdullah sai gashi a dalilin ɗan baiwa kamar yanda suka sakama Smart sun shigo cikin jerin masu nasara. Sosai London City take a hargitse yau anata selebration, su Smart na cikin wata irin doguwar mota mai masifar ƙyau da ɗaukar hankali hannunsu rike da kofin da suka ci suna ɗagawa masoya. Wasu a cikin teammate nashi har cire riguna sukai suna jefama fans. Shi kam dai murmushin sa yake mai ƙayatarwa cike da nutsuwa yana mai ɗaga hannayensa duk biyu, yayinda idan idonsa yakai kan yara yakan ma hannun nasa kiss ya hura musu, sai kaga yaran na maido masa da kisa ɗin suma, jin farin cikin yake tamkar ya zarce na cin ƙwallo a zuciyarsa yau, dan fargabar ɗazun nan da faɗuwar gaba duk ta gudu saboda addu’oin da yake ta yi. Haka suka dinga zagaye cikin London City a wannan mota, inda ta ko ina suka gitta imasoyane ƴaƴa da iyaye harma da kakanni da suka fito domin kallonsu. Sunan Smart Mawashi yasha kira a wannan rana tamkar zai ƙare duk da yanda suke kiran Mawashin abin dariya, sai yaji har hawaye na cika masa ido da wannan al’amari da rahama ta UBANGIJI. A rayuwa ai babbar rahamace ma kaga mutum ɗan uwanka na nuna maka irin soyayya balle kowa yasan Bature akan ƙyamar baƙin fata a zahirance.
Wannan fa nasara ta Smart ta saka hankalin manyan club na ƙasashen turai gaba ɗaya irinsu Italy, Spain, Germany France etc… dawo wa kansa, yayinda aketa kaikawo da cecekuce akan al’amarin yaron a wannan yini, kowacce kafar yaɗa labarai kaje a ƙasar ta England musamman a fanin ƙwallon ƙafa zancen kenan dai Smart Mawashi, Smart Mawashi.. Al’amarin kamar busa usir na alƙalin wasa. Cikin ƙanƙanƙanin lokaci manyan clubs ɗin suka fara ƙwaɗayin nuna zawarcinsa ta ƙarƙashin ƙasa……..✍️
_To insha ALLAHU dai mun kusa zuwa gaɓar da komai zai cigaba da tafiya a buɗe, ina zazu ɗin nan ne ɗan can mu samesa yanda muke so🥱 dan nasan kunfi kauri acan😜🚴🚴🚴_
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣8️⃣
………*_CANADA_*
Sosai Lulu ta riga ta sakama ranta tsoron haihuwar ne, duk yanda su Usman suka so ta haihu da kanta hakan na neman gagara. Ga naƙudar tata da gani mai zafi ce, dan tayi wujiga-wujiga a ƙanƙanin lokaci. Tun ma tana hawayen har idanun sun bushe, Ummita dai nata maimaita mata addu’a tana faɗa. Har ALLAH ya isa sai da tama Smart cikin fitar hayyaci😜, akace kuma sai anyi Shari’a da shi yayi jail😂. Abin yaso bama Usman dariya ya dai danne da ƙyar. Dr Lameer yaja Usman gefe cikin damuwa ya ke faɗin, “Ussy inaga fa muyi mata CS ɗin nan kawai, ta riga ta saka tsoro a ranta ga shi kuma jinjirin yayi girma da yawa sosai saboda ciye-ciye data dingayi. Sannan an taɓa taɓa cikin hakan ya raunana mata mahaifa. Amma da ace bata saka tsoro a ranta ba wannan bakomai bane zata iya haihuwa da kanta. Yanzu kam ina tsoron kar wahala tasa mu rasa abinda ke cikinta”.
“No no Doctor bana fatan a rasa babyn nan wlhy, inaga kawai ayi mata cs ɗin”.
“Shike nan babu damuwa, wazai saka hannu a cikinku?”.
“Bara na saka hannun kawai ni”.
Alhamdullah an samu nasarar zaro baby boy a jikin Lulu ƙamshi. Lafiyayyen yaro ƙyaƙyƙyawa da bai baro komai na ubansa ba, ga shi ƙaton gaske masha ALLAH. Dan hatta wani tawadan ALLAH da Smart ke da shi a gefen kunnensa babba shima jinjiri na da shi. Ankai Lulu ɗakin hutu, yayinda Ummita ta rungume yaro tana mai jin ƙaunarsa a ranta kamar jininta. Shi kansa Usman yaron ya shigar masa rai. Bai kira Alh. Sulaiman da ke can yana jiran ace Lulu ta haihuwa ɗa a ruɓe ba, dan yau shine target ɗinsa akan kuɓutar da su Lulun dama. Shi yay duk wani tsare-tsarensa na nemawa Lulu transper da taimakon Dr Lameer zuwa wani ɓoyayyen ƙaramin asibiti a Derby city. A wannan daren aka fita da Lulu cikin ambulance da Ummita, abinka da turai tsaro kaca-kaca hankalinsu kwance suka iso Derby city zuwa gabannin asubahi. Sanin Alh. Sulaiman zai iya bibiyarsu komai ya tafi ne akan tsari da kulawa. Dan wani gida ne a kusa da asibitin aka ajiyesu, acan gefen gari wajen ana noman fruits, sai gidan abinci da ke gaba kaɗan kasancewar babban hanya ce, sannan bature shi babu ruwansa da daji duk inda yay masa alƙarya ce. Komai da Lulu zata iya buƙata na kulawar lafiyarta su Usman ya tanada a gidan, dan bashi da damar barin ƙasar da su a yanzu kasancewar passport nasu na hannun tsule, fita dasu kai tsaye zai zama mai wahala.
Kusan ƙarfe takwas Lulu ta dawo hayyacinta, inda cikin amincin ALLAH ta farka bakinta ɗauke da addu’a. Da sauri Ummita da ke zaune a gefenta rungume da jariri dake ta barcinsa tai saurin kallonta da faɗin, “Alhamdullah aunty kin farka?”. Idanu kawai Lulun ta zuba mata ita da jaririn, sai kuma ta sauke numfashi a hankali da motsa lips ɗin ta tana mai bin ɗakin da kallo. “Ina ne nan Ummita? Miya faru da ni?”. Cike da farin ciki Ummita ta ce, “Aunty an miki C’S ne ga baby boy mun samu, nan kuma sabon wajene da Usman ya kuɓuto damu da ga hannun kawunki.” Lulu batace komai ba sai idanu data zubama jaririn hannun Ummitan, da sauri Ummita ta miƙe zuwa gabanta da jaririn, Lulu ta zuba masa ido zuciyarta na wani irin harbawa na masifa. Dan duk da yaron da sauran ɗanyantakarsa ta kasancewa jinjiri kamaninsa da mahaifinsa a bayyane suke. A hankali ta lumshe idanunta tana sakin wasu irin ajiyar zuciya a jajjere, sai kawai ta samu kanta da sakin kuka. Hankalin Ummita ya tashi, ta shiga jera mata tambayoyi akan ko wani waje na mata ciwo ne? Bata iya bata amsa ba har su Usman suka shigo, Dr Lameer ya dubata yayinda Usman ke faman lallashinta da tabbatar mata ta kwantar da hankalinta, insha ALLAH sun kuɓuta kenan, zai kumayi duk yanda zai yi na ganin sun koma gida Nigeria. Ummita ita ta bada shawaran ya kamata ama jaririn huɗuba fa, dan haka suka tambayeta wane suna take so a saka masa. Ita kanta batama san lokacin da ta furta, *_“ALIYU”_* ba. Usman da ya saki wani ɗan murmushi ya ɗauki jinjirin yaymasa huɗuba da suna ALIYU HYDAR ZAKIN FAMA. tare da masa addu’a dan duk lalacewar Usman yanada iliminsa na addini. Kawai zama a waje ne ya sashi zama mara jin magana.
Lulu da idonta ke a lumshe a zuciyarta ta furta (ALLAH ya albarkaci rayuwarka *_Aliyu Aliyu Mika’il Mawashi_*) sai kuma ta ɗan yamitse fuska kamar wadda take jin hakan banbarakwai a zuciyarta…
_(To muma dai munce ALLAH ya raya Aliyu Aliyu Mika’il Mawashi. Dangin Smart kar ace bamuyi Barka ba🥱🚴)_
*_NIGERIA_*
Sosai Daddy ke fama da ciwo a tsaitsaye, sai dai yanata dauriyar ganin bai bari ko Mommy ta fahimta ba. Sai dai ya gagara ɓoye damuwarsa akan halin da suke ciki tsakaninsa da ɗan uwansa Yousuf. Yousuf nada matuƙar muhimmanci a garesa ta yanda baki bazai iya furtawa ba. Su fa kaɗaine ƴan uwansa shi da Mommy sai zuri’ar da suka tare a yanzu. Tunda yake da ɗan uwansa bayan rikicin Kasancewar Mawaddat (Maman Lulu) a rayuwarsu baya jin akwai wani saɓani daya taɓa shiga a tsakaninsu kamar haka da Yousuf ɗin ya ɗauki zafi da shi. Ba wai baya son fitowa ya faɗa masa gaskiyar al’amari bane, bai son tada masa da hankaline kawai ko sakashi a matsala. Shiyyasa ya zaɓi shanyewa shi kaɗai a tsahon rayuwa. Amma yana gani a wannan gaɓar in har yana son ɗan uwan nasa ya fahimcesa dolene ya buɗe masa sirrin nan dai da yake ta faman biznewa a tsahon shekaru badan tsoro ba sai don dalilai guda biyu. Na farko baya son tarwatsa farin cikin family ɗin mutum mai mutunci da daraja a rayuwarsa irin Alhaji Sufi Ado Garko. Ya taka rawar gani a rayuwarsa da har a yanzu ake iya kallonsa a nuna a matsayin wane. Duk da yasan wannan rubutaccene daga UBANGIJI ko babu shi ɗin komai zai iya tabbata. Amma UBANGIJI ya sakashi zama matsayin sila. Idan ya kasance mai tarwatsa farin cikin wannan ahali yana jin kamar ya rama sharri ne da alkairi. Na biyu shine kare rayuwar yarinyarsa duk da yasan shi bai isa hana komai ba daga ƙaddarar ALLAH. Tunda gashi nan a sanadin hakan har Lulun ta faɗa shaye-shaye batare da ya iya bata kariya akan hakan ba. Hasalima bai taɓa sanin tanayi ba sai a shekarar nan. Tun daga ranar jikinsa yay sanyi matuƙa da sake tabbatar da wayo ko dabara bata kare maka abu sai UBANGIJIN talikai masanin sirrin fili da ɓoye. A hankali ya kai hannu ya ɗauke ƙananun hawayen da suka ciko masa idanu. Sai kuma ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi da ɗaukar wayarsa ya rubuta gajeren text message wa Uncle Yousuf ya tura masa, duk da yasan a gajiye yake dan jiya ya dawo daga UK kamar yanda yake ji a bakin Mommy dan shi dai Uncle Yousuf ɗin bai sanar masa ba sam.
Uncle Yousuf na tsakiyar iyalinsa suna kallo, yayinda Deen da Ra’is ke home work text ɗin Daddy ya shigo masa. Kamar zai share sai kuma dai ya ɗauka ya duba ganin kallon da aunty Saliha tai masa. Shiru yay yana kallon text ɗin da bai wuce layi biyu da rabi ba. Ya ɗan sauke ajiyar zuciya dan shima harga ALLAH yana azabtuwa da rashin ɗan uwan nasa a kwanakin nan. Dauriya kawai yake yi. Tunda ya san kansa bai taɓa wayar gari da yini harda kwana baiyi waya da yayan nasa da yakema kallon kamar mahaifi ba. Dan ko baya ƙasar sukan yi waya sama da sau uku a rana. Dan ƙa’idarsa ce duk safiya ko suna a ƙasa ɗaya ko basa nan zai gaishesa, sannan da dare kafin ya kwanta zai kirasa yay masa sai da safe. Idan ma bai kira ba bisa wani uziri na yau da gobe shi daddyn zai kirashi da kansa. Bayan wannan wayoyin biyu na ƙa’ida wasu wayoyin kan shiga a tsakaninsu game da Business ko wani muhimmin abu da ya shafesu. Jin zuciyarsa ta kasa nutsuwa waje guda ya miƙe yana kallon aunty Saliha. “Sweetheart ɗan bani key Please”. Da mamaki ta ce, “Key kuma?. Ina zakaje kaiko a daren nan kamar wanda ke a tarkon mace?”. Karan farko yay murmushin da bai niyya ba. Dan tun a kallon da tai masa sanda text ɗin ya shigo yasan akwai magana a bakinta. Komai baice ba sai wayar da ya miƙa mata. Dan tsakanin shi matarsa akwai yarda mai ƙarfi da fahimtar juna. Duk inda ƙofar zargi ta nema buɗe musu sukan yi saurin tosheta kafin a samu ɓaraka. Cikin sanyin jiki ta miƙa masa wayar da faɗin, “I’m sorry dan ALLAH, ALLAH ya bashi lafiya”. Murmushin kwantar da hankali ya mata da nuna mata hanya alamar taje ta ɗakko masa. Babu jimawa kuwa sai gata ta dawo. Ta miƙa masa tare da ɗan rungumesa. Bayanta ya ɗan bubbuga yana faɗin, “Thanks” daga haka ya saketa ya fice yanama su Deen bye bye.
Duk da dariyar dake tasoma Daddy ganin yanda Uncle Yousuf ɗin yazo a ƙanƙanin lokaci yay ƙoƙarin danneta. Sai ma sake langaɓewa da yay. Cikin sassarfa da ruɗani Uncle Yousuf ya ƙarasa garesa. Sai faman jera masa tambayoyi yake a jajjere. “Yaya mike damunka? Dama baka da lafiya? Tun yaushe kake a kwance? Kasha magani? Miyasa baka kirani munje asibiti ba?”. Cikin murmushi Daddy ya kamo hanunsa dai-dai yana kaiwa zaune kusa da shi a bakin gadon nasa. “Irin wannan tambayoyi haka a jere auta wanne zan amsa a ciki?”. Kai Uncle Yousuf ya langaɓe gefe kamar mai shirin fasa kuka, dan da gaske yaga yayan nasa ya rame masa a idanunsa sosai. Daddy ya sake sakin murmushi tare da lumshe idanunsa. Sai kuma ya yunƙura da niyyar tashi. Da sauri Uncle Yousuf ɗin ya taimaka masa ya zauna da ƙyau. Shima sai ya zauna gab da shi sosai hannayensu cikin na juna. Cikin tausasa murya Daddy yace, “Kana fushi dani saboda ɗiyarka ko? Kayi haƙuri Yousuf kaji. Yayanka ba son zuciya bace ta lulluɓe masa ido. Idan ma a kwaita to ajizancine kawai irin na ɗan adam. In sha ALLAH yau zan fiddaka a cikin duhu tun daga lokacin da kuka fara tuhumata kai da Kareema har zuwa yau ɗin nan. Amma dan ALLAH ina son kai min ƙyaƙyƙyawar fahimta kaji.”
“Insha ALLAH Yaya”. Uncle Yousuf ya faɗa a sanyaye…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣9️⃣
……..Murmushi Daddy yay masa tare da sake damƙe hannayensu cikin na juna sannan ya fara da faɗin, “Tun ranar dana wayi gari da salwantar maƙudan kuɗaɗe a cikin Company hankalinna yay masifar tashi, nabi diddigi tako wane fanni amma ban fahimci komai ba akai. Na shiga ruɗani matuƙa da tunanin ta ina zan iya samun waɗan nan kuɗi haka, dan ko za’a saida duka ƙaddarar dana mallaka a wancan lokacin bazasu biya ko kaso biyu bisa goma na abinda ya salwanta ba. Ina cikin wannan ruɗani da ɗimuwar Alh. Sulaiman ya shigo rayuwata………” kaf ya kwashe labari ya sanarma Uncle Yousuf da jikinsa ke wata irin tsuma, ga hawaye shaɓe-shaɓe kaca-kaca da fuskarsa kamar wani ƙaramin yaro. Shima dai Daddy ɗin hawaye yake, ya jawo Uncle Yousuf jikinsa ya rungume yana ɗan bubbuga bayansa alamar lallashi. Sai da yaji ya bar kukan sannan ya ɗagoshi. Zama Uncle Yousuf ya gyara cikin dasashiyyar muryarsa ya ce, “Yaya miyasa ka iya barin wannan babban al’amarin masu nauyi irin haka a ranka. Miyasa baka taɓa sanar damu ba dan ALLAH? Haba yaya har wanene Sulaiman da makircinsa da zai maka irin wannan ƙullin haka ka zauna kallonsa?”.
“Yousuf ka fahimceni hakan dolene a gareni saboda dalili masu yawa. Sannan ma lokacinne bai yiba shiyyasa, maybe UBANGIJI yay masa talalane da kuma hukuntani akan kuskurena nima. Na farko na yarda da shi da kallonsa da siffa irin ta mahaifinsa na mutumin kirki kasancewar a haka yazo min. Sannan bazan so maida sharri da alkairi ba a yanayin riƙon da mahaifin nasa yay min. Sannan dolene nayi komai domin kare ku a matsayinku na ahalina, dan shekarunka a lokacin sunyi ƙanƙantar da bazaka iya fahimtata ba yanda ya kamata. In da ban shanye komai ba za’a iya cutarmin da ku tako wace irin siga musamman ma kai, dan ko ita Kareema na hanata fita aikine daga baya bisa wannan dalilin, amma duk sai kuka fahimci cewar saboda Mawaddat ne. Eh saboda itane, dan ita ta ƙirƙiri hakan dan kuɓutar da Kareema daga sharrin Sulaiman batare da koni na fahimci hakan ba sai daga baya. Sai kuma lokaci da baiyi ba kamar yanda na faɗa, dan kasan komai na ALLAH ne sannan yanada lokacinsa.”
“Hakane Yaya na kuma yarda dakai. ALLAH sarki Maman Mawaddat munata zarginta akan abubuwa da yawa. Ciki harda tunanin ko asiri tai maka a farko, sai daga baya nima na fahimci ba haka bane saboda wasu dalilai. ALLAH ya gafarta mata ya yafe mata.”
Cikin lunshe idanu Daddy yace, “Amin Yousuf, ai shiyyasa zargi bashi da amfani. Akoda yaushe da ace munama duk wanda ya shigo rayuwarmu uziri akan al’amuran rayuwa damun zauna lafiya da samun salama a zukatanmu”.
“Hakane Yaya. Amma duk da haka akwai abinda kayi da har yanzu basu wanke a zuciyata ba. Na farko akan Mawaddat daka nisantata da samun karatun Addini dama sakaci akan tarbiyyarta. Na biyu nuna mata goyon baya akan duk abinda tai dai-dai ne harda nuna ƙyamar talaka a matsayin mijinta. Why Yaya? Bayan nasa wannan ba ɗabi’un da iyayenmu suka horar da kai bane ba”.
Ɗan jimm Daddy yay cikin tsantsar damuwa. Kafin ya ɗago idanunsa da suka kaɗa sukai jajur ya zubawa Uncle Yousuf. “Tabbas Yousuf wannan shine babban kuskuren da nai da cutar da rayuwar Mawaddat a rayuwata da bazan taɓa yafema kaina ba. Da farko halin Sulaiman ya rufemin ido da abinda naji dangin mahaifiyar Kareema na faɗa mata. Sai nake ganin nisantata da ƙasar kamar yanda mahaifiyarta ta roƙan tun farko kamar shine masalaha agareni da ita. Namanta shi UBANGIJI shine mai tsarewa a duk inda kake. Na tauye rayuwar Mawaddat akan rashin ilimin addini da kaita wata ƙasa da kafirci yafi ƙarfi a gaɓar da komai idan ta gani bazai zama abin ƙi ba a gare ta. Wannan itace jarabawata ni da ita. Maybe hakkin yarinya da Sulaiman yayma fyaɗe na ɓoye ne bayan nasan gaskiya UBANGIJI ya jarabceni da hakan, shaye-shaye kuwa a dalilin haɗa hannu da nai da su Sulaiman da bamu san iya adadin yaran da wannan safarar tamu ta gurɓatawa rayuwa ba duk da ban sani ba inaga shine nan UBANGIJI ya jarabceni akan ta. Sai kuma soyayyar da na dinga dana sani akan ƙin nuna ma mahaifiyarta har sai da ta roƙa gareta bayan ita ɗin jinina ce shima ya taka rawar gani. Sai tausayi da ya zama jagora Da silar zama komai. Ban taɓa ƙin Aliyu a zuciyata ba game da alaƙarsa da Mawaddat. Hasalima a kullum cikin tashin hankali nake kar adalilina su Sulaiman su cuta masa. Saboda har sacesa sun taɓa yi Sulaiman ya bashi aiki akanmu ni da ita. Amma yaron nan ko sau ɗaya bai taɓa gwada cutar damu ba. Yousuf baka san irin kalar ƙaunar da nakema yaron nan bane. Wlhy a duk sanda ya kawo Mawaddat gida nakan laɓe naita kallonsa da sanya masa albarka. Ko kuɗi da gida da mota dana bashi na bashine bada wata manufa ba sai don nima na ƙyautata rayuwarsa kamar yanda UBANGIJI NA ya ƙyautata tawa da silar Baba Garko, sai dai idan na fito da sigar da za’a kalla a masalaha komai zai iya faruwa da shi. Saboda yanda ya tsunduma kansa a al’amarin Mawaddat wanda na tabbatar zai iya cutuwa har sakawa nai ƴan sandan farin kaya na bin sa batare da ya sani ba. Inaga bayan aurenka ban taɓama wani aure kukan farin ciki ba sai na Mawaddat, dan a randa aka ɗaurashi na kwana yima ALLAH godiya, hakama randa ta tare na kwana roƙon ALLAH yasa gidan zamanta ne. Amma sai Kareema take ganin al’amarin nawa a juye. Ko nawa auren na farko dana biyu duk sunzo da dalilai ne, dan haka ban jisu a jinin jikina ba kamar wannan auren, ni kaɗai nasan irin addu’oi da nake maka a zuciyata. A randa na kirashi game da barinta ta fita aiki nayi hakane dan na tunzurashi da kai ku hanata fitar, dan hakan da zanyi ne kawai zai sake tabbatar min da yaron zai iya abinda nake fata akan Mawaddat. Sannan zai iya juyata a yanda kowane namiji ya kamata ya juya gidansa bawai ita a matsayin mace ta juya shi ba. Sosai na dinga dariya akan maganar da ya faɗa min, na yini raina fes, sai dai a fuska kowa ya gagara gane kaina har Kareema. Yousuf ina son Kareema sosai dan matar ƙwarai ce, sannan ita ɗin jinin jikina ce, zuciyata na mata uziri akan abubuwa da dama. Soyayyarku a gareni ta dabance Yousuf, ku nakema kallo tamkar iyayena, dan kuna iya gayamin gaskiya duk ɗacinta. Garama Khareema tana jin shakkata, wasu lokutan takan haƙura ta shanye”
Shiru kawai Uncle Yousuf yay yana kallon Yayan nasa da murmushi a fuskarsa mai ƙayatarwa, a zuciyarsa kam sai ayyana (Namijin duniya) yake. Tare da jin nadamar abubuwan da ya dinga yi game da ɗan uwan nasa musamman zargi. Cikin ƙarfin hali Daddy ya katseshi da tambayar ina Smart yake a yanzu?. Kai tsaye Uncle Yousuf ya sanar masa komai akan Smart daya sani da ga wajen Abdull-Hameed Coach. Sosai Daddy yaji tausayin yaron ya ratsa masa zuciya, tare da ƙaunarsa ta haƙiƙa na sake ratsashi…
“ALLAH ya bashi nasara akan burinsa ya kuma yimasa albarka” Daddy ya faɗa yana miƙawa Uncle Yousuf wayarsa. Uncle Yousuf dake amsa addu’ar Daddyn ya amshi phone ɗin ya tsirama hoton ƙyaƙyƙyawan jaririn ido, tunani yake ina ma yasan wannan fuskar?. Kasa hasasowa ya sashi faɗin, “So cute Yaya, yaron wanene haka da nake jinsa a raina tamkar jininmu”. Murmushi Daddy yay mai haɗe da ƴar dariya, sai kuma ya dafa ƙafaɗar Uncle Yousuf ɗin da faɗin, “Jininka ne Yousufa. Dan ka zama Grand father yanzu”.
“Grand father? Ta yaya Yaya? Ni da bayan Mawaddat ɗina ban aurar da kowanne ɗa ba, duk da itama an sanar mana tana da ciki, sai dai rashin sanin ina take yasa bama musan yaushe ne haihuwarta ba”.
Sake faɗaɗa murmushin Daddy yay da tsare ƙanin nasa da ido dan san ganin irin reaction ɗin da zai nuna. A hankali ya furta, “Ai Mawaddat ɗin taka ce ta haihu jiya ɗin nan…”
“What!!!!”.
Uncle Yousuf ya faɗa da ƙarfi cikin wata irin zabura da ta saka jikinsa har yana karkarwa. Cikin rawar murya ya ce, “Yaya Please karka min wasa irin wannan dan ALLAH. Wlhy zan iya maka kuka”.
Dariya sosai Daddy keyi masa, kafin ya jinjina masa kansa alamar tabbatarwa. “Babu wasa a maganata Yousuf, bakaga ɗan na maka kama da ƙanin naka Aliyu ba.”
“Ya subahanalillah! Yaya dan ALLAH mafarki nake ko ido biyu? Idan a barci nake jin wannan zancen ka taimakeni karka bari na farka. Idan ko a zahiri ne ka faɗamin dama kasan inda Mawaddat take duk wannan kaiwa da komowar da nake yi”.
Daddy dake murmushi har yanzu ya kamo hannun Uncle Yousuf ya sake zaunarwa a kusa da shi. “Please relax sweet heart. Ai ina sane da duk wani shigi da ficinka, na Barka ne har zuwa irin wannan ranar ta yau sannan kasan gaskiyar al’amarin. Dan na sanka da rashin haƙuri farin ciki zai iya sakawa ka buɗe min aiki. Ai tun a randa Dada ta tabbatar min Mawaddat na’a wajenta na ƙara tsananta bibiyar Sulaiman. Saboda na tabbatar duk inda Dada zata kaita sai da gudumawarsa. Nace maka na tafi Hong Kong ne kawai dan na ɓatar da kowa a lissafi, da ga can na bibiyi Sulaiman ƙafa ya ƙafa har zuwa ƙasar Canada da ya nufa shi da ɗansa. Ban wani sha wahala na a bibiyar tashi ba na gano inda Mawaddat take. Sai dai ban zauna ba na kamo hanya na dawo, tare da jin ƙarfin gwiwar barinta cikin ƙudirar UBANGIJINA. Sai dai na saka wani yaro Usman ɗan Alhaji Bashir Sa’eed dake Canada cigaba da bibiyar min al’amarin su dama na gidan gaba ɗaya. A bakinsa naji Mawaddat na ɗauke da ciki, har ma da kaita asibiti da sukai domin yunƙurin zubar da shi, da ceto cikin da yay har zuwa yau……..” kaf ya kwashe komai da ya sanar masa. A abin mamaki sai ga hawaye share-share Uncle Yousuf na sake zubarwa. Daddy ya cigaba da faɗin, “Ina kan sani na barta can a wajen nasu duk da nasan Sulaiman zai iya cuta mata, sai dai kasancewar Usman na sanar min duk wani motsinsu ya sani sake samun ƙwarin gwiwa. Nasan hakan shine kawai zai sake koyama Mawaddat sabuwar rayuwa ta fahimci mi ake nufi da gundarin rayuwar ma kai tsaye. Ta kuma san wanene Sulaiman ta yanda duk sanda za taji komai game da shi abin bazai zo mata a bazata ba balle harta cutu. Sannan zata sake sanin muhimmancin mijin da darajarsa tare damu family nata gaba ɗaya. dan a yanzu haka Dada ta sanar mata mijinta ya saketa”………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣0️⃣
………Ji Uncle Yousuf keyi kamar yay ta kuka, ga wani jin zafi da takaicin Dada da Alh. Sulaiman na cimasa zuciya. Sai sake kallo Jaririn yake a hotuna harda ɗan gajeren vedion. Uncle Yousuf ya rungume Daddy jikinsa na tsuma. Babu wanda ransa ke hango masa kamar Smart a yayinda zaiji wannan labari mai cike da al’ajabi da mamaki. Dan koda Dada ta sanar musu samuwar ciki da kasancewarsa basu faɗa masa ba saboda yana kan gaɓar da kwanciyar hankali yafi buƙata, ga shi su kuma ba sanin inda zasu samo Lulun sukai ba a lokacin balle su ƙarfafa shi.
“Yaya yanzu yaushe zata dawo gida? Dan tana buƙatar kulawa a yanzu sosai”.
“Ya sake kwashe musu passport ɗinsu ne shiyyasa, amma ina kan ƙoƙarina na son ganin an dai daita musu komai sun baro ƙasar. Sai dai ba Nigeria nake so ta dawo ba, dan ina son nai amfani da wannan damar ne wajen ɗaure Sulaiman da jijiyoyin kansa sannan na ɓata abinda na gyara akan Mawaddat.”
“Wannan tunani ne mai ƙyau Yaya, inaga kawai ta wuce wajen mijinta to”.
“Zan so hakan Yousuf, sai dai zai iya zama matsala. A yanzu yaron yana a wata gaɓa ne da kowa zai iya kai masa hari ya kumayi tasiri a kansa cikin sauƙi. Bai kamata mu bada gudunmawar maida shi baya ba bayan al’amura sun ɗakko hanyar warware wa. Su Sulaiman shu’umai ne ta yanda komai zasu iya aikatawa. Sannan suna huɗɗa da manyan ƴan iskan duniya a fagen cinikayyar kayan shaye-shaye. Wannan babbar dama ce a hannunsu da akowane ƙasa mutum yake, ko wane irin matsayi ya taka zasu iya ƙulla masa. Abinda kawai ya dace muyi yanzu shine mu rufe bakunan mu ruf zuwa wani lokaci, amma mahaifinsa da mahaifiyarsa su san da wannan haihuwar. Shima kuma na aika a sanar masa yanzu hakan. Daga iya mu huɗun nan kar kowa yasan inda Mawaddat take Please”.
“Na fahimceka ƙwarai da gaske Yaya. Kuma insha ALLAHU a yanzu bakai kaɗaine zakai wannan aikin ba. Ni da kai ne zamuyisa dan na fara ji a jikina Sukailan ne ya koyama Mawaddat shaye-shaye”.
Sosai Daddy yaji daɗi da farin ciki, duk da yana tsoron kar a cutar masa da ɗan ƙanin nasa ɗaya tilo kuma. Amma ya bar komai a hannun UBANGIJI, sannan idanunsa a buɗe suke a yanzu kam kowane irin ƙalu bale ya shirya masa. Zancen Alh. Sulaiman ne ya koyama Lulu shaye-shaye kuma shima kansa yana wannan tunanin, a yanzu haka kuma yana kan bincike ne sosai har ma da yanda akai Nanny ɗin Lulun ta mutu duk zuciyarsa na masa zargin Sulaiman. sai dai a yanzu bai cema Uncle Yousuf ɗin komai akan hakan ba….
*_CANADA_*
Sosai Alhaji Sulaiman da ya iso Canada yau ɗin nan ke a cikin tashin hankali. Dan duk iya bincikensa yayi amma babu Usman babu su Lulu. Har asibitin da aka kaima Lulun cs yaje sai suka ce masa su basuyi wata theatre wa mai sunan ba. Neman haukace musu yayi, daga ƙarshe akasa security fiddashi tare da warning ɗinsa mai ƙarfi na in ya sake dawowa yay musu hayaniya zasu saka jami’an tsaro kamashi. Baya haɗa sabga da jami’an tsaro ko’a Nigeria, dan kun san mai kaza a aljihu baya jimirin ass. Balle ya samu labarin mahaifinsa ya saka a bincika a nemo inda yake tun kusan wata uku da suka wuce. Shiyyasa ma yaƙi zama waje guda yaƙi kuma shiga Nigeria kwata-kwata duk da labarin da ya samu har na sakin mahaifiyarsa Dada da Baba Garkon yayi. Yana tsaka da kasancewa a haukacensan saƙo ya iso masa. A birkice ya saka hannu a littafin ɗan saƙon, tun kafin ya koma cikin gida ya buɗe, inda ya fara cin karo da hotunan ƙyaƙyƙyawan jariri har kala uku. Hoton ƙarshe da ke ɗauke da rubutu ya juya cikin tsumar jiki. *_Zakaran da ALLAH ya nufa da cara, ko ana mazuru ana shaho sai yayi. Aliyu Aliyu Mika’il Mawashi ya iso duniya lafiya_*
“What!!” Ya faɗa cikin bugawar ƙirji da rawar hannu. Sai kawai ya saki wani irin ihu mai ƙaraji tare da yin watsi da hotunan. “Usmaann!!” ya sake ambata da ƙarfi. Sai kuma ya ƙyalƙyale da wata irin dariya mai ƙona zuciya, tare da faɗin, “Yaro baka san wuta ba sai ka taka. Ka taro babban match ɗin da kaf family naka basu isa zamar maka defenders ba. Sai na tarwatsa rayuwarka ta inda zaka dawwama dana sanin yaudara ta da ka shirya yi. Yarinyar kuma da hannunka zaka maidota gareni”. Da ga haka ya fisgi rigar sanyinsa da ke a hanger ya fice gidan…..
*_NIGERIA_*
Tun randa taji Smart baya Nigeria ta kasa zaune ta kasa tsaye, ko kaɗan zuciyarta da gangar jikinta sun gagara hutawa. Ba ita kaɗai ba, hatta ƴaƴanta ta cusa musu hassada da ƙyashin da ya ingizasu fara bibiyar al’amuran Smart har suka gano irin cigaban da yake samu a yanzu haka, duk da dai a farko dariya suka fara da ganin Smart ɗin ai a ƙaramin team yake ma. Sai dai kuma a hakan ma dai UBANGIJI sake bayyana shi yake ga duniya a bisa kowane matakin nasara koda akwai ƙalubale a cikinsa. Abu na biyu yanda Abba ya fara jiƙewa a ƙanƙanin lokaci, dan bai iya ɓoye alkairin da Smart ɗin ke turo masa. Duk da ba wasu maƙudan kuɗi bane na tashin hankali, sai dai suna riƙesa ta yanda a yanzu haka baima fita kasuwa sai yaran. Duk da aikin da Malam Na-zuru ya sake mata a kan Smart ɗin hankalinta ya kasa kwanciyar jiran nashin kaɗai. Tuni sun bazama ga wasu malaman harma da bokayan babu inda Hajiya Naqiba bata zuwar mata. Wani lokacin kuma suje tare ma.
Ammah ce ta fara fuskantar al’amarin na Umma a randa ta kamata tana bizne abu a bayan windown ta ga sunan Smart tana kira. Hankalin Ammah ya tashi matuƙa a wannan ranar, amma bata yarda Umma ta ganta ba harta kammala. Bayan barinta wajen tai kiran ƙanwarta Gwaggo Sa’adah ta sanar mata komai cikin tashin hankali. Gwaggo Sa’adah ta kwantar mata da hankali akan tana zuwa, sai dai karsu taɓa abinda Umman ta bizne tunda akwai jinin Smart a jikinsu. Gwaggo Sa’adah ce tazo da wani almajirinta, inda cikin hikima ya tone abinda Umman ta bizne ɗin. Layune da wasu sirkulle a kwalba an ɗaure. Koda aka kunce layun abinda ke rubuce a ciki su dukansu ya daga hankalinsu. Amma sai almajirin nan ya ce su kwanatat da hankalinsu addu’a tafi gaban komai ai. In sha ALLAH tunda an farga da wuri babu abinda zai faru, zai je da su ya lalata. Gwaggo Sa’adah taso a ajiye a nunama Abban. Amma sai Ammah tace a’a a ƙyaleta a rufa mata asiri idan halintane zata ƙara ai har Abban ya gani da kansa wataran. Har Gwaggo Sa’adah taji haushi sai kuma da ga baya ta fahimci hikimar Ammah.
Tunda ga faruwar wannan al’amari Ammah ta sake dagewa da addu’a akan ƴaƴanta gaba ɗaya. Tare da sadaka akoda yaushe. Duk inda taga maraya tana ƙoƙarin taimaka masa. Suma yaran kullum cikin ƙara ƙarafafasu take da ibada har Smart. A duk sanda sukai waya sai ta sake nusar da shi. Alhmdllh yana fahimtar ta sosai, kuma dama baya sakaci akan ibadarsa duk da wataran gajiya kan hanashi iya tashi sallar daren daya sabama kansa yanzu. Amma a koda yaushe bakinsa bai rabo da ambaton ALLAH.
Yau ma kamar kullum gidan yana ruɗe da hayaniyar yara da jikoki kasancewar juma’a ce ta ƙarshen wata. Dan an sakko massalacin kenan sai ga Abdull ya shigo yana sanarma Ammah Abbah yace a bada ruwa anyi baƙi. Kasancewar itace da girki babu wanda ya damu. Ta haɗa ruwa harda zoɓon da Maryam tayi domin zuwan Ahmad ɗinta kasancewar duk juma’a yake zuwa hira bayan sallar la’asar (Kun san fa Ahmad da Maryam an jone🥱). Har Abdull zai wuce Ammah ta sake dakatar da shi, dan tunda taga Abbah ya aiko a amshi ruwa da alama baƙin masu muhimmanci ne. Masar da tayi matsayin abincin rana ta zuba ta ce Asma’u ta ɗauka ta bisa da shi.
Sosai Uncle Yousuf ya tsirama Asma’u da ta kai har ƙasa tana gaishesu idanu, dan sosai tana kama da Smart, sai dai kawai dan shi namiji ne ita mace, ta kuma fishi haske sosai. Murmushi yayi domin tuna wani abu. Daddy na lure da shi sai dai baice komai ba har Asma’un ta fita. Mikewa Abba yay da nufin barinsu suci abinci, amma sai Daddy ya ce yayi zamansa ai ruwama kawai ya wadar. Ɓata rai Abba yay da faɗin, “Saboda abincin namu ba irin naku bane Alhaji Isma’il?”.
Cikin ɗan daburcewa Daddy yace, “Wlhy ba haka bane Malam Mika’il. Amma aimana afuwa bara muci.” dariya suka ɗanyi cikin barkwanci, da ga haka suka shiga buɗe abincin, ganin masa tasha manshanu ga lafiyayyen zoɓo bama su san sanda suka shiga cin ba har sai da suka tada abincin tas. Daddy na tsokanar Uncle Yousuf ne ya cinye, shima yana tsokanarsa shine ya cinye. Shi dai Abba dariya yake musu cike da sha’awar wannan zuminci tamkar wasu abokai. Bayan sun kammala Uncle Yousuf yace ya kamata Ammah tazo dan suji miya kawosu a tare. Abbah ya jinjina kansa cikin gamsuwa, sannan ya ɗaga waya yay kiran Ammah. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gata, tayi mamakin ganin ashe baƙin su Uncle Yousuf ne, amma sai batace komai ba ta zauna suka gaisa cikin girmama juna. Uncle Yousuf ya zaro hotuna a aljihunsa ya miƙama Abbah. Amsa yay yana murmushi, sai dai yana kallon jinjirin dake a hoto sai da zuciyarsa ta harba. Dan haka ya ɗago da sauri ya na duban Ammah data tsira masa ido, sai kuma ya dubi su Daddyn da ke kallonsa da murmushi. Itama dai Ammah gabanta ne ya faɗi lokacin da taga abinda ke jikin hoton, muryarta na rawa ta ɗago tana kallon Abbah. Abban Salim wannan ai Hydar ne yana jinjiri, sai dai ban san sanda aka ɗauki hoton ba gaskiya, dan kayama na manta da su.”
Daddy da ya kasa riƙe dariyarsa ne yay gyaran murya, dan haka suka dubeshi su duka har Uncle Yousuf dake danne tasa dariyar shima. Daddy ya ce, “Anya Aliyu ne? Kudai sake kallon hoton Malam Mika’il”.
Kallon juna Ammah da Abba suka sake yi, sai kuma suka sake maida hankalinsu a hotunan. Abba ne ya sake cewa, “Gaskiya Aliy ne a hotunan nan Alhaji Isma’il. Ba mu da muka haifesa ba ma, duk wanda zaka tambaya in har yasan Aliy yana jariri wannan amsar zai baka”. Ammah dake jinjina kai tace, “Wannan gaskiya ne Abban Salim. Dan Hydar ne yana jariri”.
“Wannan jinin Aliyu Hydar ne a yau ba Aliyu yana jinjiri ba”. Cewar Uncle Yousuf cikin murmushi. Cikin haɗa baki Abbah da Ammah sukace, “Jinin Aliyu! Tayaya?”.
“Ta hanyar matarsa Baba. ALLAH ya albarkaci matar Aliyu da haihuwa jiya, wannan shine albarkar da ALLAH ya azurtamu da ita mu da ku da shi”.
A hankali hawaye suka ziraroma Ammah da jikinta har yake tsuma. Muryarta na rawa ta ce,…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣1️⃣
……..“ALLAHU akbar, ALLAH mai rahama mai jin kai, Sarki gagara misalin masu misalai. Isashe mai iko da koman da ke iya kallon kansa a iko. Dama anga ɗiyar tawa?”.
Kai Uncle Yousuf ya jinjina mata, da ga ita har Abbah da farin ciki ya sashi jin yama kasa motsawa, sai sunayen ALLAH yake ambata a jajjere. Cikin nutsuwa Uncle Yousuf ya zayyane musu komai ta yanda zasu fahimta. Wato gano inda Lulu take dama abinda ya faru akan cikin har zuwa haihuwarsa a yanzu. Sai dai suna roƙonsu da su ɓoye wannan sirrin dan basa son asan inda Lulu take a yanzu har sai abubuwa sun dai-daita domin koyama Alh. Sulaiman da Dada hankali bisa kuskurensu. Da ga ƙarshe suka sanar musu sunan yaro Aliyu kamar yanda Lulun ta saka aka masa huɗuba da shi. Sosai su Ammah sun gamsu da wannan dabara, tare da mamakin wannan baƙin hali na su Dada. Ga kuma Umma a gefe itama tana nata yaƙin, duk da dai Ammah ce kaɗai tasan da wannan. Yaro yasha addu’oi shi da mahaifiyarsa Lulu na fatan samun lafiya a gareta. Da ga ƙarshe Daddy yace musu su shirya domin sama musu visa dan yana son suje su gano Jariri. Da farko Abbah yaso ƙi, acewarsa bazasu sakasu wahala ba. Duk randa suka dawo Nigeria ai zasu ganshi. Amma sai Daddy da Uncle Yousuf sukaita roƙonshi. Da ƙyar dai ya yarda ya amince. Inda tun a ranar suka fita da su domin yin passport. Abinka da harkar kuɗi, an gama musu duk abinda ya dace cikin ƙanƙanin lokaci saura jiran result kawai.
Kowa ya kalla Abba da Ammah a wannan yinin yasan suna cikin farin ciki mai tsanani, sai dai ba’a san kona minene ba. Dan hatta su aunty Bilkisu Ammah bata sanarmawa ba sai Gwaggo Sa’adah kawai saboda ita ɗin sirrinta ce, ai ko sai ga Gwaggo Sa’adah itama da hawayen farin ciki, da yammacin nan bata iya haƙuri ba sai da tazo gidan taga hoton jariri. Ita Umma dama bata gidan, tana can wajan biɗar baƙar tambayarta. Bata dawo gidan ba sai yamma lis. Sannan su Abba har sun dawo da ga fitar da sukai. Amma sai Mama ta sameta har ɗaki da gulmar wai yau surukan Smart sunzo gidan, kuma sun fita da su Ammah tana ganinfa akwai matsala. Sai dai kuma su Ammah tunda suka dawo sai faman washe haƙora sukeyi da ga ita har Abba. Dan Ammah harda su sadaka tayima yaran anguwa da maraicen nan. Sosai wannan magana ta tsayama Umma a rai, dan sabon malaminta da sukaje wajensa a yau ɗin nan dama ya sanar musu akwai wani babban al’amarin farin ciki da ya samu Smart ɗin, sai dai ya gagara gane ko minene anata nuna masa haske kawai babu komai. Amma taje gida duk abinda taji gobe ta dawo. Sai kuma gashi da ga dawowar tata taji sabon zance a wajen Mama macijin sari kanoƙe. Cikin matsanancin tashin hankali tai kiran Hajiya Naqiba suka tattauna, sai dai duk iya hasashensu sun kasa canko komai ilai tunanin ko Lulu zata dawo ne. Amma dai sun tsaida matsaya Umma taje ta zunguri Abbah akan batun. Wannan shawarar ta rika, dan haka a daren dan ta kasa nutsuwa ta nufi ɗakin Abba da nufin su gaisa tunda yau bata yini a gida ba. Lokacin Ammah ta baro ɗakin da kwanikan da yaci abincin dare. Zaman dirshen Umma tai suna hira da Abba bayan sun gama gaisawa, inda cikin salon makirci ta fara zungurarsa da batun Smart duk da bata fito fili ta ambaci sunansa ba. Dai-dai nan ALLAH ya kawo Ammah, tsaf ta fahimci manufar Umman, dan haka ta zauna a falon dan tasan halin maza wani lokacin sai addu’a musamman idan suka haɗu da makirar bace. Zuwan Ammah baima Ummah daɗi ba sam, dan tasan halin Ammah da shegen tsartar tsiya. Dan haka ta tashi ta fice cikin jin takaici tana ƙwafa. Da kallo kawai Ammah ta bita tana girgiza kai, inda bayan sunbar falon zuwa makwanci cikin hikima ta sake nusar da Abba muhimmancin ɓoye al’amarin haihuwar nan kamar yanda su Daddy suka roƙa, Abba ya fahimceta sosai, sannan bai zargi tayi hakane saboda Umma ba dan Ammah mace ce mai hikima da dattako. Kawai dai dan ba fitinanniya bace da lallai su Ummah sun kaɗe a gidan nan…..
*_UK LONDON_*
Sosai yake cikin farin ciki mara misali, yaso yay amfani da ɗan hutun da suka samu yazo gida Nigeria sai dai hakan na neman gagara saboda kara kainar da manyan clubs keyi akan al’amarin sa. Duk da dai abin bai fito fili duniya ta fahimta ba Coach ɗin sa shi da komai ke a garesa da Manager ɗin sa Uncle Yousuf suka ce ya dakata dai aga inda wasan zai tsaya. Wannan shine dalilinsa na haƙura da zuwa gida Nigeria ya cigaba da bama kansa hutu a gidansa. Sai motsa jiki da yakan fita da ɗan yawata gari idan yaso a wasu lokutan.
Yau ma yana gida kwance a binsa, sai dai idanunsa biyu yana zaune ne a falo idonsa a tv yana kallo sai popcorn da ke gefensa yana jefa ɗaya-ɗaya a baki (Su Smart an zama an gayu😂😜🚴). Gift da wani ɗan lutin yaro ke buɗewa a film ɗin yana tsalle ya sashi tunawa da saƙon da aka kawo masa jiya da yamma da ko buɗewa bai yi ba. Hasalima tunda ya amsa ya ɗora shi a inda takalmansa suke farkon shigowa falon bai sake bi ta kai ba dan yasan dai bai wuce irin gift da fans nasa kan kawo bane takanas garesa. Miƙewa yay a hankali zuwa corridor ɗin farkon shigowa, saƙon na’a inda ya barsa, dan haka ya ɗakko ya koma falon. Kiran Ahmad da ya samu na shigo masa a waya ya sashi ajiyewa ya ɗauki wayar. Kamar yanda suka saba cikin barkwanci suka gaisa da juna, Ahmad ya sake masa congratulations da tabbatar masa da next month yana tafe fa, dan yana son yazo ya masa hutu. Sun ɗan ja lokaci suna hirarsu cike da nishaɗi da ƙaunar juna kafin suyi sallama. Har ya sake shagala da batun saƙo zai koma ya kwanta sai kuma idonsa ya sake sauka a kai. Tashi yay ya jawo brown envelope ɗin ya buɗe tare da zira hannu a ciki ya zaro kayan ciki. Hotuna ne har guda biyar, sai flash drive guda ɗaya da kwalin haɗaɗɗen turare designer ɗan ƙarami sai masifar ƙamshi. Hotunan dake a kife ya fara ƙoƙarin dubawa, haka kawai ƙirjinsa na wani irin harbawa, saukar idanunsa akan hoton farkon sai da zuciyarsa ta motsa da ƙarfin gaske a cikin ƙirjinsa. Tsigar jikinsa ta shiga wani irin ya mutsawa. Tabbas wannan duk wanda ya sanshi a jinjiri yaga hoton nan yasan shine, sai dai shi da kansa yasan bashi ɗin bane ba saboda dalilai da yawa idan aka auna, musamman yanayin hoton da inda aka ɗauki hoton da suturar jikin yaron duk da yasan duk za’a iya editing, cikin tsumar jiki yaje ga hoto na biyu, nan ma dai yaron ne again. Hoto na uku ma haka, sai a na huɗu ne fuskar da bazai taɓa mantawa ba ko’a magagin barci ce rungume da yaron a saman ƙirjinta tana da ga kwance jikinta ɗaure da zanin asibiti, ga ƙarin ruwa a hannunta, sai rabin jikin mace da ke gefenta ta dafe mata yaron sai dai ba’a ganin fuskarta. Hajijiyar da yaji tana neman kwasarsa ta sashi komawa a kujerar daɓar ya zauna. Da ƙyar harshensa ya iya motsawa wajen furta, “Mawaddat da jariri ta yaya?”. (Ta yanda kowa ke samu mana) zuciyarsa ta bashi amsa kai tsaye. Rawa lips ɗinsa ya shigayi da illahirin jikinsa, dan sam ya kasa furta abinda ma yake son furtawar. A dai-dai nan kira ya shigo wayarsa. Da ƙyar ya iya juyawa ya duba wayar. Uncle Yousuf ya gani ɓaro-ɓaro. Cikin zallo kuwa ya caɓi wayar dan gani yake kamar mafitace ALLAH ya kawo masa na warwarewa da ga ruɗanin da ke neman zauta masa ƙwaƙwalwa tamkar a mafarki…
“Congratuletions angon ƙarni”.
Kalmar farko da Uncle Yousuf ya furta masa bayan sallama da ta daki ƙirjinsa. Da ƙyar ya iya furta, “Angon ƙarni Uncle?”.
“Yes of course Son. Ka zama Daddy mana, na kuma san saƙon yaya zuwa yanzu ya isa zuwa gareka sai dai in baka duba ba”.
Wasu irin hawaye ne da masifar gudu suka shiga biyo kumatun Smart. Muryarsa na rawa ya furta, “Uncle kana nufin da gaske ne Mawaddat nada ciki kuma ta haihu? Sannan kun san inda take”. Uncle Yousuf da ke murmushi da ga can ya ce, “Hakane Aliyu, ALLAH ya azurta Mawaddat da samun ciki, kuma an mata cs a jiya an ciro yaro mai kama da kai, sai dai muma da ga baya duk muka san hakan. Tsaf ya kwashe labarin su Dada dana Daddy ya sanar masa har yunƙurin zubar da ciki bai ɓoye masa komai ba. Ya ɗora da bashi haƙurin cewar an ɓoye masa maganar ciki ne a lokacin dan kar a tada masa hankali tunda basu san takamaiman ina Mawaddat take ba a lokacin ɗin sai Daddy shi kuma ya ɓoye ne dan tsaron lafiyarsu, tare da manufarsu ta son a ɓoye yanzu har sai an wajiga rayuwar Alh. Sulaiman. Ɗari bisa ɗari Smart ya yarda da wannan shirin, yayinda zuciyarsa ke masa kai-kawo akan sakkowar Daddy da sauri haka. Sai dai baicema Uncle Yousuf komai game da wannan ba. Ya daiyi murmushi da cema Uncle Yousuf batun Alh. Sulaiman wannan wasan nashi ne. Jin wai Lulu kuma tace a sakama yaron sunansa ya sakashi sake yin murmushi da lumshe idanunsa, dan harga ALLAH baiyi tunanin hakan daga gareta ba. Irin farin cikin da Smart ke ciki yau da banne a rayuwarsa, dan ko randa sukaci nasarar cin ƙwallon nan baya jin farin cikin sa yakai koda kwatar haka. Ya kira Abbah da Ammah cikin zumuɗi, inda suma suketa tsokanarsa cike da farin ciki tare da masa barka da arziƙi. Ya ce, “Ammah shiyyasa kullum sai naita mafarkin yara, ashe takwarana yana isarmin da saƙon ya kusa zuwa duniya ne”. Dariya Ammah keyi, cikin tsokanarsa ta ce, “Oh ni Hydar ko irin ƴar kunyar ɗan farin nan babu ma?”. Dariya ya ƙyalƙyale da shi tare da rufe fuskarsa da fillon kujera kamar yana gabanta, ya ce, “Ammah sai anjima to nayi shiru”. Itama dariyar ta shiga yi masa sosai cike da jin shauƙi da tarin ƙaunar tilon ɗan nata namiji……..✍️
_🚴🚴🚴Yau fa dangin Smart an cika mu da iyayi, to ɗa dai bara mu bada ba ehe dan zufarmu ce😏_
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣2️⃣
……..Koda ya ajiye wayar miƙewa yay zuwa cikin bedroom ɗin sa. Alwala yay domin gabatar da nafilar godiya wa UBANGIJIN talikai mai ƙyautar da kuɗi ko ƙarfin mulki baya badawa a duniya. Gaskiya tunda yake a rayuwarsa baya jin an taɓa masa wani suprice mai taɓa zuciya da jijjiga jinin jiki irin na yau. Bayan ya idar ya jima yana kwararoma ɗan nasa da Lulu kanta addu’oi, tare da fatan ALLAH ya kawo musu dai-daiton wannan al’amari da ƙarshensa cikin sauƙi su cigaba da rayuwa a inuwa ɗaya tamkar sauran ma’aurata. Wayarsa ya sake ɗauka ya dawo falon.
A karan farko Smart yay kiran number Daddy yau tunda yabar Nigeria. Sun gaisa cikin mutunta juna da nuna jin nauyin juna musamman ma shi Smart ɗin. Daddy ne ya fara masa barka, shima Smart ɗin yay masa barkar. Da ga haka Daddy ya bashi haƙuri akan abinda duk ya faru a baya da masa bayanin akwai dalilin yin hakan, zai masa bayani amma ba yanzu ba sai sun haɗu. Sai batun ɓoye masa ciki da inda Lulu take nan ma ya bashi haƙurin kamar yanda Uncle Yousuf ya bashi da masa bayanin dalilin yin hakan. Cikin girmamawa Smart ke roƙon Daddy da ya daina bashi haƙuri shi bai taɓa riƙesa a ransa ba ko ganin laifinsa. Yana masa kallon uban ne da kuma uzuri dan yasan koma minene yanada dalili, ya kuma fahimci hakanne tun a randa Alh. Sulaiman yasa aka satoshi, shiyyasa ma ya haƙura da halayen Lulu ya sake komawa aikin gidan. A yanzun ma yana roƙon Daddyn da ya bar wannan wasan a hannunsa ya kwanta ya huta ya haifa masu masa yaƙin ai, fatansa kawai in har bai shiga hurumin daba nashi ba yana son jin tushen matsalar ne kawai. Murmushin jin daɗi Daddy yayi da ga can har Smart yana iya jiyosa. Da ga haka ya shiga sanya masa albarka da tabbatar masa in sha ALLAH zai sanar masa komai, sannan ya ɗauki kansa matsayin ɗa a garesa koda wasa ya daina jinsa daban a cikin family ɗin sa. Bama shi da suka haɗa jini ba a yanzu ko ahalinsa sun zame musu ahali ai suma. Sosai Smart yaji farin ciki da waɗan nan kalamai na Daddy, tare da sake jin kimarsa da mutuncinsa a zuciyarsa.. da ga haka sukai sallama cikin mutunta juna.
Bayan sun ajiye wayar Smart ya ɗakko laptop ɗin sa ya saka flash ɗin nan a ciki. Ba komai bane face videon yaronsa mai tsananin kama da shi sai Mawaddat ɗinsa da keta kallon jariri tana wani munafukin murmushi tare da motsa lips ɗin ta sai dai baya iya jin mi take faɗa, sai matashiyar matar da ke gefenta tana tofama yaron addu’a. A hankali ya lumshe idanunsa da sakin wata irin raunananniyar ajiyar zuciya ƙwallar ɗinbin farin ciki na sake cika masa idanunsa. Shi yama rasa mizaiyi domin nuna farin cikinsa akan wannan ƙyauta ta UBANGIJI mai tsadar gaske da kuɗi ko alfarma bata badawa a wannan duniya.. ji yake inama zai iya tauntsuwa ya gansa gabansu, kai shi koda muryarta ne yaji ma ta waya zai rage masa nauyin zuciya. Ƙasa haƙuri yay ya turama Uncle Yousuf saƙo akan neman number ta. amma sai ya samu reply cewar babu waya a hannunta amma akwai ta yaron da ya kuɓutar da su mai suna Usman zai tura masa. Duk da ya ɗan ji kishin nasa ya motsa sai ya danne…
*_NIGERIA_*
Sosai ta yi wata irin rama data sake bayyana tsufarta sosai gamai kallo. Ga shi bata da isashiyar lafiya sakamakon tsangwama da rashin kulawar da take fuskanta a hannun matar ɗan nata. Ba komai ya jawo hakan ba kuma sai gara rayuwar surukan nata data jima tanayi a shanun talla. Musamman ma ita matar Uncle Manner ɗin. Itama kuwa sai gashi ALLAH ya bata damar ramawa. Abinda yafi yima Dada ciwo a zuciya makircin Hajiya Aneesa, dan in har Uncle Manner na gida bai isa gane komai akan matar tasa ba, kulawa take bama Dada kamar uwarta mahaifiya, amma yana gusawa kashi ma ya fita daraja. Ta dinga gasa mata azaba da magana kenan masu zafi har sai hawaye sun cikama Dada ido. Ga shi ta hana ƴaƴanta raɓar Dadar sai ubansu na nan, daga bayama ko uban nasu na gida sai basa zuwa, da tayi magana kuma za’ace makaranta ce ta ɓoye su. Kaɗaici da damuwa sunma Dada yawa, ga kewar mijinta da rashin ƴancin data saba dashi na tsawon shekaru, babu irin kalar kiran da bataima Baba Garko da tura masa saƙo ba amma tamkar ma baya ganinta. Abinci kuwa sai wanda aka gadama ake bata dan nata daban ake dafa mata garo-garo su kuma suci lafiyayye. Idan Uncle Manner ya gani kafin ma yace wani abu matarsa ta fara zayyana masa zancen Dada ce tace ai mata, sunyi-sunyi kuma ta kafe harda musu tsiya. Sanin halin mahaifiyar tasa da yayi da irin hantara da ƙyarar da takema matar tasa tunba yanzu ba saya baya maida hankali ko ƙin yarda. Idan kuma ta saka masa kuka da nuna son ita dai a canja mata gida ko’a roƙar mata mijinta sai zuciyarsa na bashi son komawa wajen baban nasu ke damunta kawai. Yakan zauna yay mata nasiha da nuna mata illar biyewa zuciya da ɗan uwan nasa da tayi, yanzu gashi nan ya barta a halin ƙaƙa nakayi, tunda ko Nigeria ya ƙi zuwa, hasalima yaji ƙishin-ƙishin tattare iyalinsa da yake shirin yi su bisa inda yake a ɓoyen saboda tsoron umarnin mahaifinsu akan duk randa ya diro ƙafarsa Nigeria tun a airport a kamashi. Ga kuma tashin hankalin rashin sanin ina Lulu take a yanzu. Dan zuwa yanzu ta gama tabbatar ɗan nata nada manufa akan al’amarin da nasa. Ga Baba yasa an cafke Tajuddeen da ya shigo Nigeria a watan daya gabata, saboda bakinta daya furta cewar tare da shi ake komai ai. Iya binciken Tajuddeen anyi amma ya rantse shi bai san ina ubansa ya kai Lulu ba, ya dai san da su ake komai da farko amma shima kansa bai farga akwai wata manufa a ziciyar mahaifin nasa ba sai bayan na son ya aura masa ita. Sai a randa ya rabosa da Canada ya kwashe su Lulun. Ya kuma rantse a yanzu bai san ina yake ba, dan ya ɓoye kansa ne. Amma sam Baba Garko yace bai yarda ba, ƴan sanda su cigaba da riƙe Tajuddeen ɗin har sai Alh. Sulaiman ya miƙa kansa koya sako Mawaddat. Baba Garko yayi hakane kuma dan ya jima da sanin Tajuddeen shine zuciyar ɗan nasa. Kamar kuma ya sani dan hankalin Alh. Sulaiman na can a tashe game da kama masa yaro, dan haka ya baza mutanensa suketa shige da ficin ganin an saki Tajuddeen ɗin amma hakan ya gagara. Dan Baba ma da babansa, duk ƙarfin ikon da suke jin suna da shi da alfarma a ƙasar Baba Garko ya taka su ya shanye. Wani lokacin ma da bazarsa yake rawa.
Waɗan nan abubuwa marasa daɗi sunka haɗu suka tararma Dada a zuciya dan haka sam ta kasa lafiya. Ga shi a lissafinta wannan watanne na haihuwar Lulu in har Alh. Sulaiman bai salwantar da cikin ba kamar yanda yay niyya tun farko, sannan iddarta ta kusa cika, tana cika kuma hakan na nufin sun rabu kenan, dan tasan irin kafiyar Nana garko, sai idan da rabon su koma ne ma sai an sake ɗaura mata aure da mijin nata na auren tun jajayen sawu. Kwanciyarta asibiti kusan uku a tsakanin nan, a yanzu hakan ma tana asibitin tun shekaran jiya ƙarƙashin umarnin likita, sai banka mata allurar barci suke dan ta samu nutsuwa…
★Tsaf Alhaji Garko na biye da al’amarin matar tasa, kuma ya maida aurensu tun a randa ya saketa kodan tausayin yaransu. Amma ya zaɓi yin biris da ita dan lamarin jikar tasa na ci masa zuciya. Ya kuma ɗauki alƙawarin hukunta ɗan nasa akan wannan al’amarin. A yanzu haka ya baza cid suna kan bincika masa inda yaje ya ɓoye kan nasa, dan yanaji a jikinsa a duk inda yake Mawaddat tana tare da shi….
__________★
Kamar yanda bokanta ya sanar mata ta koma sai da tai yanda tayi wajen hillatar Abba ya sake barinta fita yau suka koma ita da Hajiya Naqiba. Sun gurfana a gabansa suka gama masa bayanin komai, cikin jinjina kai da bugun ƙasa ya ce, “Tabbas akwai ɓoyayyen al’amari kuma iyayensa sun sani, sai dai an gargaɗesu da sanar wa kowa shiyyasa sukaja bakinsu sukai shiru. Kamar yanda na sanar muku tun farko bawai yaron zai gagaremu bane, kawai dai tsaye yake da ƙafafunsa wajen bautama ALLAH tamkar mahaifiyarsa. Bata gajiya kuma da nusar da duka ƴaƴanta ta wannan fannin. Shiyyasa cin galaba a kansa kamar baya abune mai wahala. Amma zamu gwada sa’armu mu gani a yanzun ma sai dai akan matarsa duk da itama tana nata ƙoƙarin . Sai dai maganar gaskiya ban gano abinda zai iya tasirin rabashi da nasarar da ke tunkarosa ba game da abinda yake yi ɗin. Dan lokacin hakanne yayi. Kunsan ance mai laya kiyayi mai zamani. Abinda kawai zan iya muku aiki a kansa shine nisanta shi da al’amarin matarsa itama kuma a nisantata da duk abinda ya shafesa, wannan zai iya zauta masa zuciya ƙila har al’amarin ƙwallon nasa ma ya iya taɓarɓarewa duk da dai abune mai wahala hakan ta kasance. Sannan kuma ko akan wannan farraƙun tsakaninsa da matarsa in ma anci nasarar sake nisantasun fa na gano akwai haɗari a ciki, kuma haɗarin zai iya dawowa ne matsayin ƙaiƙayi koma kan masheƙiya gareki. Yaya kika gani ayi ɗin?”.
Ɗan jimmm Umma tayi yayinda Hajiya Naqiba ta zuba mata ido da mata signal ɗin ta yarda kawai babu abinda zai faru ai sune masu nasara. Wannan ƙarfin gwiwar data hanga a idanun aminayar tata ya sata jin jina ma malamin nasu kai da faɗin, “Babu ma abinda zai faru malam in sha ALLAHU. Ni in sansamu ne ma har uwarsa da uban ai musu kalar asirin nan dan na tsani buɗe ido naga Hafsatu a gidan nan wlhy, sauran sakarkarun basu daman ba, dan babu wacce tasha gabana sai ita. Na rasa wane shegen boka ke mata aiki haka”.
Murmushi malam yayi kawai. Sai kuma zuwa can ya nisa da cewa, “Maganar iyayensa gaskiya bamai yiwuwa bane kamar yanda na faɗa miki. Dan matar nan a tsaye take fa wajen bautama ALLAH. Ke dai kawai ai miki na yaran ma zai baki duk nasarar da kike buƙata in har ba’a samu kuskure ba”.
“Bama za’a samu ba malam ayi kawai.” Hajiya Naqiba ce mai maganar. Malam ya amsa musu da to, tare da gaya masu adadin kuɗun da aikin zaici, babu musu ta ajiye masa duk da da ƙyar ta ƙwaƙulesu a hannun Salim, sai da tasha ƙunƙunai ma da ƙananun magana sannan ya bata. Amma da yake tana so haka ta amsa tana sanya masa albarka……
Koda ta koma gida dukkan yanda akace mata ta aiwatar tayi cikin kulawa da taka tsan-tsan, daga haka ta koma gefen kallon yaya wasan zai fara kuma………✍️
_(Ni dai nace Hummm Ummah kenan🚴😵💫)._
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣3️⃣
………*_CANADA_*
Kwanaki Uku kenan da mata cs ɗin, amma Alhamdullah da alamun fara samun lafiya tattare da ita kasancewar bata da ƙan jiki, sai dai kuma Lulu akwai raki. Mahaifiyar Usman da yake kira da Mamy tazo tana tare da su tun shekaran jiya. Hakan yasa take sake ƙara samun kulawa ita da jinjirinta. Ga Ummita na iya ƙoƙarinta itama tako wane fanni. Hakama Usman da Dr Lameer. Tayi mamaki matuƙa da ganin ɗunbin kayan baby da Mamy ta kawoma Aliyu ƙarami. Sai dai yanda matar ke kulawa da su cikin haba-haba ya sa Lulu kasa cewa komai akan hakan. Duk da wannan gata da kulawar da take samu wajen abokan arziƙi zuciyarta a cinkushe take da rashin ahalinta ko guda ɗaya a kusa da ita. Hatta shi kansa uban tafiyar yakan zo mata a rai, duk da a duk sanda yazo ɗin takan yamutse fuskar cikin nuna halin ko’in kula. Sai dai hakan babu alamar zai turesa a ran nata, dan data dubi ɗan jaririn nata zuciyarta kan harba mata, balle kuma idan tana shayar da shi takan zuba masa idanu da tafiya cikin tunani mai zurfin gaske akan al’amarin mahaifinsa. Kasancewar Mamy babbar mace ta jima da hango halin da Lulun ke a ciki, amma bata cewa komai saboda lokacin cewar bai isa ba…
A ranar da su Lulu ke cika kwanaki biyar da zuwan baƙon duniya su Abba da Daddy suka iso ƙasar Canada, tafiyar da tai masifar tada hankalin su Ummah dan Abba yace musu zasuje duba Smart ne zuwa ƙasar England. Jidali iya jidali rasar su Aunty Amarya sun gani wajen Ummah, dan su Asma’u ma basa gidan Ammah catai su tafi gidan yayunsu har sai sun dawo su dawo. Dan haka suka tafi gidan Aunty Bilkisu da shirin idan suka mata kwana biyu sai su koma gidan Hawwah itama su mata kwana biyu. Babu irin zagin da Ammah bata sha ba ranar har maƙwafta sai da suka shigo, inda mutane da yawa suka fara fassara al’amarin Umman da hassada. Dan sukam basu ga wani abin tada jijiyar wuya a nan ɗin ba…
Oho su Ammah ma basu san tana yi ba, dan suna can a hanya hankalinsu kwance. Ƙasar England su Abba suka fara yada zango wajen Smart. Wanda zuwan nasu yazo masa a bazata sosai, dan sam Uncle Yousuf bai sanar masa ba. Tsabar farin ciki baima san lokacin da ya rungume Ammah ba. Turesa tai cikin jin nauyi da faɗin, “Kajimin ja’irin yaro abinda ka koya a ƙasar turawan kenan kuma?”. Cikin dariya da shagwaɓa Smart ya ce, “Ammah nafayi missing ɗinki ne, ALLAH sai nake ganin kamar mafarki nakeyi”. Tsinguli ta kai masa da faɗin, “Bari na tabbatar maka idonka biyu”.
“Ouch!” ya faɗa cikin turɓune fuska yana kallon Abba a marairaice. Abba ya riƙo masa hannu yana hararar Ammah. Daddy da Uncle Yousuf dai dariya sukeyi, dan basu taɓa zaton Aliyun taɓararre bane a wajen iyayen nasa sai yau. Smart ya gaishe da Daddy cikin girmamawa, Uncle Yousuf kam ai baida maraba da aboki duk da yanzu ana ƴar kunyar surukuta kaɗan-kaɗan. Sosai mazaunin Smart ɗin ya ƙayatar da su Ammah, suka shiga godiya ga UBANGIJI a zukatansu da mamakin wannan rahama ta UBANGIJI. Sunci sun sha daga abincin da Smart ya tanada musu a cikin ƙanƙanin lokaci, dan abinci ne na ƴan Nigeria. Bayan kowa yaci ya ƙoshi suka ɗan tattauna, sosai zaman ya sanyaya ran Smart, inda ya fahimci surukinsa sosai a yanzu ya kuma sakko daga fushin daya tafi. Sun tafi zuwa masauki aka bar masa Ammah da Abbah nan. Hakan ya musu daɗi su duka, dan sun sami damar tattauna abinda ya shafesu sosai shi da iyayen nasa. Inda ya ƙara warware musu cigaban da ya samu da wanda yake fatan samu anan gaba. Ƴan uwansa kaf bai manta da kowa ba sai da ya tambaya, har maƙwafta da abokan arziƙi. Ranar dai ansha hira, dan duk rashin yawan maganar Ammah da Smart yau dai sun sha hira abinsu kamar suyita kasancewa a haka suke ji…
Washe gari da yamma suka wuce Canada har da Smart dake jin wani irin faɗuwar gaba lokaci-lokaci, yakanyi sauri ya ambaci sunan ALLAH. Wannan ziyara tazo ma Lulu a bazatar bazata. Dan bata san wainar da ake toyawa ba sai kawai ganin Usman tai da baƙi. Lokacin da suka shigo tana toilet ne ita da Mamy dake gasa mata jikinta da towel kamar dai yanda ake cikakken wankan jego a Nigeria duk da Lulu tasha maganin da ya dace Mamy bata barta ba kullum sai ta mata safe da yamma ita da ɗan jinjiri.
A hankali take tafiya Mamy biye da ita, tayi fayau da ita sai haske data ƙara da wani cikar ido irin na jego dan tana samun kulawa sosai irin ta malam bahaushe a wajen Mammy duk da cs akai mata. Alhamdullah kumburin ciki da tai duk ya saɓe amma baza’a kirata ramammiya ba kai tsaye. Sanye take cikin doguwar riga mara nauyi dake a buɗe sosai saboda yanayin inda aka yanka ta. Baya tai zata faɗi saboda firgicin ganin abinda idanunta suka gane mata, sai da Mamy ta riƙota tana faɗin, “Mawaddat yi a hankali kinji”. Daga lips ɗin Lulu har zuwa jikinta rawa yake yi, ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallo tun daga kan Daddynta har zuwa mutum na ƙarshe da ke tsaye ya ɗan jingina abango da harɗe ƙafafunsa waje guda. Sanye yake cikin Suit milk da sukai masifar masa ƙyau da fitar da cikar haiba da kamalar da ya ƙara, ga wani irin ƙamshi mai sanyi da daɗin shaƙa, gaba ɗaya ya canja da ga Smart na Nigeria zuwa wani baƙin bature mai aji a yanzu. Yanda yay tsaiwar ƙasaita da harɗe ƙafafunsa waje guda idanunsa a waya yana daƙila kamar baya a wajen saika rantse ba shine ke zumuɗin azo ba fiye da kowa. Sai da Mamy ta ambaci sunan Lulu ne ya ɗan ɗago idanun nasa a hankali da take kira na macizai kamar zai lumshesu sai kuma ya zuba mata su cikin shammata da bazata.
Wani irin girgiza zuciyarta tayi ƙirjinta na bugawa da sauri-sauri. Rashin mafita ya sata juyawa cikin tsumar jiki ta basu baya tana mai rumtse idanunta da masifar ƙarfi. Ammah ce ta taka a hankali zuwa gareta, cikin tausayawa da ƙauna ta kira sunanta. Kasa juyowa Lulu tayi sai jikinta da ke ƙara ƙarfin rawa. Riƙo hannunta Ammah tayi ta juyo da ita a hankali, sai kaiwa ta faɗa jikin Ammahn ta rungumeta tsam-tsam tare da sakin kuka mai tsuma zuciya.
A hankali Smart ya sauke idanun nasa ƙasa yana wani irin haɗiyar zuciya da sauri-sauri. Dai-dai nan Ummita ta shigo ɗakin da sallama bayanta goye da baƙon duniya dake barci. Turus tai tana kallonsu itama cikin tsoro da mamaki, yayinda su kuma suka zubama jinjirin bayanta ido. Uncle Yousuf ne yay ƙarfin halin mata nunin ta kunto yaron. Sai ta kalli Mamy. Kai Mamy ta jinjina mata alamar ta kuntosa babu matsala, dan haka ta ɗan saki ajiyar zuciya tare da kunto yaron ta miƙama Uncle Yousuf ɗin. Kamar ko ya sani sai ga idanu ya ɗan buɗe yana motsa baki alamar neman abinci. Dariya Uncle Yousuf ya saki da faɗin, “Oh oh Aliyu dai kawai ne anan babu wani banbanci wlhy sai na shekaru”. Yay maganar yana ƙarasawa gaban Abba da Daddy cikin sassarfa. A hankali Smart da idanunsa ke kan yaron ko ƙyaftawa babu tun shigowar Ummita ya wani lumshe idanun da suka kaɗa a hankali yana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Jin al’amarin yake kamar a mafarki, shi Aliyu Hydar ne da ɗa na mutum matsayin mallakinsa a wannan duniyar. Ya arrahaman ALLAH mai alkairi. Furucin Lulu da ke faɗin, Ammah nayi kewarku cikin kuka ya sashi buɗe idanun nasa ya zuba musu su. Murmushi Ammah da ke sharema Lulu hawaye takeyi, kafin ta kama hannunta ta ƙarasa da ita a saman gadon da take jiyyar. Dai-dai nan Abbah ya ƙarasa da Jinjirin ga Smart, nannauyar ajiyar zuciya Smart ya ja tare da fesarwa, sai yaji ma duk ya sake daburcewa. Fahimtar hakan da Abbah yay ne ya sashi sakin ƙaramar dariya da sake miƙa masa yaron. A hankali ya miƙa hannayensa duk biyu Abba ya saka masa yaron a ciki, sai da yay masa kallon kusan sakanni goma kafin ya matsar dashi saman ƙirjinsa ya rungume tsam-tsam dai ga hawaye sharrrr. Uncle Yousuf dake murmushi ne ya ƙaraso gareshi, cikin tsokana ya ce, “A’a ƙanina kaga zauna karka zube mana a ƙasa majiyatan su sake ƙaruwa kuma”.
Furucin Uncle Yousuf ɗin ya sata sake ɗago idanu a karo na biyu ta kallesa, sai akai sa’a shima ita ɗin yake kallo har yanzu yaron na’a rungume jikinsa sai dai ya share hawayen. Harara ta balla masa da ɗauke kanta tana tura baki. Sai ya samu kansa da sakin murmushi yana wani ƙasa-ƙasa da idanu shima. Ammah da ke ankare da su su duka ta ce, “Babana zo mana naga sabon uba dana sake yi, danni kam kai da Mawaddat kun zama Kakannina yanzu kam tunda kun haifa mini Babana”.
A hankali ya tako gaban Ammah cikin yanayin nan nasa na nutsuwa da kasancewa jarumin namiji tsayayye. Maimakon ya miƙama Ammah babyn sai ya kai zaune a kujerar gaban gadon kusan da Mawaddat da hankalinta ke kan Uncle Yousuf da ke mata magana ƙasa-ƙasa…..
Bayan an gaggasa Lulu ta gama ma Daddy da Uncle Yousuf shagwaɓa da koke-kokenta suma sukai mata faɗa akan barin ɗakin mijinta tabi Dada. Ta basu haƙuri da amsar kuskurenta. Sunji daɗin nuna nadamar tata kuwa a gaban kowa. Duk alkairin Ummita da Mamy da Usman gareta bata ɓoye ba. Su Abba sukai musu godiya sosai da wannan karamci duk da akwai sannaya tsakanin mahaifin Usman ɗin da Daddy. Bayan komai ya natsa an fahimci juna Usman yay ma su Abba jagora zuwa masauki, har lokacin kuma bakin Lulu da Smart bai saɓa ba, sai dai ƴar satar kallon juna, koda yake ma shike satar kallon nata, itako tayi biris kamar ta ma manta da shi a ɗakin take nunawa. Baiji komai a ransa ba game da hakan dan halinta kuma ai sai dai ya bama wani labari yanzu. Lulu akwai jan aji, koda wasa bata yarda ta zama a ƙasa ba akan al’amarinta. Lokacin da zasu wuce Usman ya ce ai shi Smart a barshi anan tare zasu wuce gida, suje su ya fara kaisu masauki sai ya dawo ya samesa. Mamy da Ammah kam dama tuni sun fice zuwa ɗayan ɗakin gidan. Itama Ummita sai ta zare jikinta cikin dabara wai bari ta wanke kayan baby data jiƙa ɗazun. Harara Lulu data fara tsarguwa da wannan ƴar zare jikin da ake ɗai-ɗai tabi Ummita da shi, sai dai batace komai ba dan Ummitan ta fita tana mata dariya………..✍️
*_😂Kar naji wani yace komai kuma ehe. Musamman ma dangi dangi Smart ɗinnan. 🙈Koda yake akwai su aunty fa🚴🚴_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣4️⃣
…….Shiru ɗakin yay bakajin komai sai ɗan ƙarar room hitter kasancewar sanyin da ake zubawa. Zaune yake cikin kujerar nan cike da ƙasaita ɗansa rungume a jikinsa ya zuba masa idanu kawai tamkar mai son gama haddace halittar jikinsa gaba ɗaya. Yayinda ita kuma take zaune a gadon jiyyarta ta miƙe ƙafafunta dake cikin blanket hannunta riƙe da sabuwar tab da Usman ya siya mata jiya. A zahiri wayar take kallo da sarrafawa, sai dai a ƙasan zuciyarta mamakin irin canjawar da Smart ɗin yayi take har yanzu, tamkar fa ba drivern nan nata ba, ya wani goge ga tsadaddun kaya wanka iya wanka, koda yake tun ma yana a drivern sa ita shaida ce ya san sirrin saka kaya, sai dai na yau ɗin dabanne, dan ko faratansa ka kalla kasan ya samu canjin rayuwa. Dama can bamai hayaniya bane shi, amma yanayin nasa na yanzu ya sake sakashi a wani matsayin zafafan maza masu aji da jan ajin. Kai itafa ALLAH da’ace a hanya taga mutumin nan maybe bazata iya shaida shi ɗin bane ba duk da kamaninsa na nan a tare da shi, sai ƙyawu da kwarjininsa mai bayyana cikar kamala da haiba da ya sake bayyana. Numfashi taja a hankali ta fesar, sai kuma taja ƙaramin tsoki da ya sakashi ɗagowa a hankali da ga kallon babyn nasa da yake yi ya sauke mata firgitattun idanun nasa da take kira na macizai. Duk da bashi take kallo ba sai da tsigar jikinta ta tashi ta kuma ji kaifinsu a cikin jininta. Sai kawai ta sake ɗaure fuska.
Cikin son ta kallesa da deep voice ɗin nan tasa acan ƙasan maƙoshi ya furta, “Ashe haka kika ɗauki darasin nan nawa da gaggawa ɗaliba ta? Ai ban san ke ɗin zaki kasance duka ɗauka ba haka, ga result na first class na gani kam”.
Sosai ta danne zuciyarta wajen nuna masa tamkar bama ta jisa ba balle ta fahimce shi. Amma duk da haka sai da ta ɗan saci kallonsa ta gefen ido. Wani murmushin ƙasaita ya saki tare da miƙewa ɗauke da babyn ya isa zuwa gareta, kafin tayi wani yunƙuri ya kai zaune a bakin gadon har jikinsu na gogar juna. Babu wanda baiji shock a jikinsa ba amma kowanne ya basar. Kaifafan idanun nasa ya zuba mata yana mai kai hannunsa ya ɗago haɓarta ta yanda zai kalla fuskarta sosai da ƙyau. Suna haɗa ido sai kawai ta lumshe idanun nata da ture hannunsa zuciyarta na wani irin harbawa, ita kaɗai tasan mi take ji game da shi, amma bata so tayi giving up, not now. Ƙoƙarin sake riƙo fuskar tata yake yi ta buge masa hannu a karo na biyu.
Murmushi yayi mai sauti, tare da faɗin, “Baki son gani na ne?”.
Ba tare data sake iya kallonsa ba a tunzire ta ja tsaki da faɗin,, “Aliyu bana son damuwa, wannan rayuwa ta ce, ka fita kamar yanda na buƙata tun farko please. In ma saboda wannan ɗan kazo kasa a ranka baka da alaƙa da shi, koma kana da ita to yafi ƙarfinka danni da ga yau da ga yanzu na datse alaƙar taku har abada.”
Wani irin murmushi ya saki mai ƙayatarwa tare da tsurama babyn ido, sai kuma ya ɗago yana kallonta cikin lumshe idanunsa da buɗesu duk a lokaci guda. Cikin murya mai taushi ya ce, “Mawaddatan’warahmah! Kin taɓa ganin inda aka raba jijiya da ƙashin baya aka cigaba da rayuwa akan ƙafafu? Duk wanda ya kalla wannan ajiyar ALLAHn yasan zufan Aliyu Hydar Mika’il Idris Mawashi ne ai. Shi ɗin jinin jikina ne, ke da kika haifa min shi kuwa jijiyar ƙashin bayana ce, taya kike tunanin zan rayu a lokacin da babu jini a jikina babu lakar ƙashin baya? Please ki kalla cikin ƙwayar idanuna ko sau ɗaya ne, maybe ki karanci abinda ke a cikin zuciyar Aliyu Hydar ɗin ki. So ɗaya yake miki tak da in sha ALLAHU wata mace bazata sake samun kwatankwacinsa ba. Ko so kike sai na kai ƙasa gaba ɗaya zaki yarda da ni?…”
Harga ALLAH kalamansa sukarta suke. Sannan yamutsa mata illahirin jinin jikinta sukeyi. Duk wani ƙwarin gwiwar ta a garesa neman suɓucewa takeyi. Cikin sanyin jiki da rauni ta ɗago idanunta cike da ƙwalla, sai dai bata iya kallon cikin nasa idanun ɗin ba kamar yanda ya buƙata ta maida su ta duƙar.
“pleaseee!”.
Ya faɗa a hankali cikin wani irin salon jan “e” ɗin ƙarshe data saka tsigar jikinta mimmiƙewa gaba ɗaya. Sai kawai ta samu kanta da sakar masa kuka da faɗin, “I say live me alone please Aliyu. Kace ka sakeni bayan ka keta min haddi akan abinda na bada tsahon shekarun rayuwata na hankali ina karewa, mi kuma ya rage da kake buƙata a gareni yanzu? Ko ɗan numfashin da ya sauramin kuma shima so kake sai ka rabani da shi zaka huta? Ka barni dan ALLAH, ka cigaba da zama a nesa da ni ni yafi min I beg you” ta ƙare faɗa cikin haɗe hannayenta waje guda alamar roƙo🙏.
A hankali ya kwantar da yaron gefe ɗaya, tare da matsawa kusa da ita. Jikinta ta janye baya tana sake fashe masa da kuka. Ƙoƙarin riƙota yake tana buge masa hannu. Bai damu ba ya riƙota ya saka a jikinsa ya rungume tsam. Tana ƙoƙarin masa magana cikin kuka da fisge-fisge ya hanata kowacce irin dama ta hanyar manne lips nashi cikin nata. Wata irin nannauyar ajiyar zuciya ya saki yayinda ita kuma ta sake sake masa kuka da san ƙwatar kanta. Sai da ya tabbatar ya saka jikinta yin laushin da ta daina ƙoƙarin raba jikinta da shi sannan ya saketa dan jikinsa ya fara karɓar al’amarin. Da sauri taja jikinta gefe ta dunƙule waje guda tana faɗin, “Mugu ALLAH sai ya sakamin”.
Murmushi yay da lumshe idanunsa ya buɗe a kanta. A nutse cikin firzar da huci ya ce, “Muguntar mi nayi ni da halalina kuma. Mawaddat believe me duk wanda ya faɗa miki na sake ki ƙarya yay miki, har abada Aliyu bazai taɓa rabuwa da Mawaddat ba koda ana min azaba da bulalai ina tuɓe a tsakkiyar sanyin ƙanƙara. Har abada Aliyu zai cigaba da kasancewa matsayin mijin Mawaddat ne koda bazata cigaba da rayuwa da shi ba.”
“Aiko dole ka rabu dani, dan inada kalar mijin da nake so in ma auren zanyi amma ba irin ka ba”.
“Ohh just keep your mouth up Mawaddat! Idan ma mafarki kike to ki farka wlhy, kuma duk sanda kika sake ambatar min kalmar wani namiji na rantse miki sai na darje waɗan nan silly lips ɗin naki ta yanda bazasu sake buɗuwa da sunan magana ba”. Ya faɗa cikin hasala da birkice mata tamkar wani bajimin bahagon matashin zaki. Har Babyn da ke a gefensu yana barcinsa na ɗan zabura shima dan tsorata. Da sauri ya ɗaukesa ya mannasa da jikinsa yana mai lumshe idanunsa da suka kaɗa sukai jazur a ƙankanin lokaci. Duk tsaurin ido irin na Lulu ita kanta sai da ta firgita. Dan tsantsar tartsatsin wutar bala’in kishi ta hango a cikin birkitattun idanun nasa. Ta gefen ido ta saci kallonsa, dan ya miƙe yana jijjiga yaron saboda mutsu-mutsun da ya cigaba da yi. Ganin ya fara ƙushin-ƙushin ɗin kuka ya dawo gabanta cikin takun ƙasaita da hasala. Saman cinyarta ya ajiyesa babu alamar wasa a tattare da shi cike da bada umarni ya ce, “Shayar min da yaro abincin sa”.
Ɗago idanunta data ƙanƙance tai cikin hasala da mamakin ƙarfin halinsa. Sai dai hararar da ya wurga mata cikin tashi hasalar ya tabbatar mata wannan fa ba Aliyun baya bane data saba yima yanda taso. Sai ma duk taji tana neman daburcewa. Shiko ganin bata da niyar bama yaro abinda yace kawai ya kai zaune gab da ita kansa tsaye ya tura hannunsa a rigarta ya fiddo, zaro idanunta tai a wani irin razane, sai dai shi ko’a jikinsa dan kallo ma bata ishesa ba hidimar gyara yaron yake da ƙyau ya saka masa a baki. Shiko ɗan albarka ya cafke abinsa da sauri har sai da tai ƴar ƙaran jin zafi. Sai dai ta gagara ture uban da ɗan dan duk ya kanainayeta ga numfashinsa da ke sauka a jikinta wani irin harmutsa mata lissafi yake neman yi gaba ɗaya. Da ƙyar ta iya fisgo kalmar, “Aliyu wai miye haka bana son wulaƙanci f…..”.
Fuskarsa ya matsar gab da tata ta yanda ta kasa ƙarasa abinda ta faro faɗar, ya wani busa mata iska a fuska da wata irin murya acan ƙasan maƙoshi ya furta, “Naga dai namu ne ai ni da shi. Dan haka bama son hayaniya karmu ƙware”.
“Takaici, haushi, kunya, duk suka kanainaye Lulu a lokaci guda. Ga wani irin neman rikita mata lissafi da kusancin nasu ke neman yi. Shima kansa a wahalen yake da kusancin nasu, dan da ƙyar yake danne zalamarsa da haɗiyeta….. Lips ɗinta da ke rawa-rawa ta buɗe zatayi magana sallamar Ummita ta katse ta, Ummita da ta shafa’a da kasancewar sa a ɗakin bata jira an amsa mata ba ta shigo, hakan ya sashi jan jikinsa baya da gyara mata yaron cike da basarwa. Ita ma Ummitan sai tai saurin juyawa zata koma cikin ruɗewa tana faɗi, “Ya ilahi dan ALLAH kuyi haƙuri, wlhy na shafa’a”.
Smart ne cikin ɗan furzar da iska mai nauyi ya furta, “Karki damu dawo abinki”. Badan Ummita taso ba ta dawo, sai dai kanta a ƙasa ta ajiye bowl ɗin data shigo da shi mai ɗauke da gasashen nama da yaji kayan haɗi da Mamy ke haɗama Lulun duk bayan kwana biyu. Zata juya Lulu dake hararar baby da babansa ta dakatar da ita da faɗin, “Ummita anko samo zam-zam ɗin?”.
Kanta a ƙasa ta ce, “Eh Yaya Usman ya sayo tun ɗazun ai, harma da zumar”.
“Yauwa dan ALLAH haɗo a fidarsa kin sanshi ba ƙoshi yake ba ya gado ci irin na ub….”
Sai kuma ta kasa ƙara sawa ta murguɗa baki kawai. Murmushi Smart ya saki, a hankali ya furta, “Ai dama ƙyawun ɗa ya gaji Ubansa. Baki ji har sunan bai bari ba ya gado. Ashe haka kike son sunan nan amma baki taɓa faɗa min ba?”.
Harararsa tai cikin takaici tana jin kamar ta shaƙurosa. Sai dai batai magana ba dan sai ma yanzu take jin haushin kanta da tace a saka mata sunan. Baki Smart ya taɓe kaɗan shima da ɗaukar bowl ɗin naman ya buɗe, guda ya cira da ɗan tsinken da aka sako a ciki ya kai baki yana lumshe ido. Hakan ya saka Lulu zuba masa nata idanun batare da ta lura da abinda take yin ba har ya buɗe nasa da suka wani ɗan shanye tare da yin luww kamar mai jin barci. (He looks so handsome) zuciyarta ta ayyana mata. A fili kam sai tai saurin fara janye nata tana wani taɓe baki. A kasalance shima ya janye nasan yana jan ajiyar zuciya………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣5️⃣
…….Sai kawai ya miƙe zuwa jikin window ya ƙurama waje idanu yana kallon shuke-shuken fruits da ganyayyakinsu ke sake ƙawata ƙamshin wajen. Da ƙyar ya iya samu ya dai-daita kansa a wajen har Ummita ta shigo ɗauke da zam-zam mai haɗe da zuma a ɗan wani kofi da ƙaramin spoon. Tana ajiyewa bata zauna ba ta fice. Nannauyar ajiyar zuciya ya sake sauke a karo na babu adadi da takowa ya dawo gaban gadon, komawa yay ya zauna a inda ya tashi tare da amsar yaron data janye a jikinta tana gyara riga. Amsarshi yayi yana goge masa baki, ita kuma sai ta miƙe masa ɗan cup ɗin. Cikin ɗan tura baki a ranta tana faɗin (Kaima ka ɗan ɗana wahalar da nake ci a kansa)
A mamakinta babu musu ya amsa. Kamar kuma dama can wanda ya saba da rainon cikin nutsuwarsa ya ɗibo ruwan zam-zam ɗin mai haɗe da zuma ya zubama yaron a baki kaɗan sai gashi yana ɗan motsa bakin da yamutsa fuska. Hakkanne ya saka Smart sakin murmushi har ya ɗago ya kalli Lulu da itama dai kallon nasu take yi. Kauda idanun nata tai ta maida kan bowl ɗin namanta ta fara ci. Cikin ɗage gira ya ce, “Wannan dai ƙwaɗayinki ne ya gado Madam”.
Da sauri ta ce, “Wa ɗin? ALLAH ya sawwaka mi muka haɗa da shi da zai gado ni, haɗuwa a duniya rabuwa a cikinta”. Sosai maganar tata ta bashi dariya, amma sai baiyi ba yay murmushi kaɗan yana girgiza kansa. Ganin yasha sosai ya goge masa baki ya gyara masa kwanciya a ɗan gadonsa. Lulu ya kama tana kallonsu, amma yana juyowa ta kauda kanta gefe. Kusa da ita ya koma ya zauna gaf, batare da yayi magana ba ya amshi tsinken da take cin naman ya tsira shima ya kai bakinsa, sake tsiro wani ya kai mata baki, idanunta ta zuba masa batare data buɗe bakin ba, shima kallon nata yake a yanayin kasala, dan haka ya ɗan lumshe nasa idanun da kaɗa mata kansa alamar ta amsa. Kamar mai jin ciwo akan lips ɗin ta motsa su da ƙyar shi kuma ya saka mata naman. A kusan tare suka sauke nannauyar ajiyar zuciya su duka. Da ga haka ya cigaba da bata yana ci, sun ci kamar lauma uku a bazata ya jeho mata tambayar da ta sakata ɗan daburcewa, amma jarumar taku sai ta dake abinta.
“Mi yasa kika zaɓi yin rainon cikin nan ke kaɗai batare da ni ba?”.
Cikin basarwar nan tata da son dakewa batare data kallesa ba ta ce, “Miye haɗina da kai da zamuyi rainon ciki tare?”.
“Mai ciki da abunsa har ace miye haɗinsa da cikin. Serious banji daɗin haka ba Mawaddat. Naso ace Ni ne da kaina na kula da ke tamkar ƙwai a cokali a wannan gaɓar. Ban taɓa fuskantar minene ainahin ƙunci ba sai da na waiga babu ke a duniyata, nasan har yanzu zuciyarki na baki na aikata miki abinda ya faru a wancan ranar bisa son zuciya. Ko kaɗan ba haka bane, dan ina son kasancewa da ke basai na baki komai ba ai, domin ke ɗin halalina ce, mizai sa saina wahalar da kaina ta hanyar gusar miki da hankali kamar wani matsoraci. Kin taɓa ganin Aliyu Hydar a matsayin KURE ba ZAKI ba?”. Harararsa tai, sai dai ta kasa cewa komai, shima sai ya ɗan murmusa kaɗan da cigaba da bata naman yana faɗin, “Duk abinda ya faru a wannan ranar Ahmad ne ya ƙullasa bada sani na ba, sai dai karki damu zan rama miki ai kinji ƴar ƙanwata”.
Cikin suɓutar baki da harararsa akan ƙanwarsa daya kirata tana waro idanu ta ce, “Ahmad fa? Taya zan yarda hakane?. Sannan akan Maryam ɗin? Zaka rama?”
“To mata tafi mata ne? Shi ya jawo mata ai. Duk da dai ni ya biyani tunda ban wahala a banza ba ga AA Mawashi na a kusa da ni”. Karan farko tai kamar zata saki murmushi sai kuma ta hararesa ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Sai ka shirya amsa hakan a gaban alƙali ai. Dan sai an bimin kadin hakkina na fyaɗe”.
“Shima alƙalin koroki zaiyi da ga gabansa ai. Nidai yanzu nace magana ta wuce kawai, Aima Abbien AA afuwa bazai sake yin fyaɗe ba”.
“Humm” ta faɗa tana mai lumshe idanunta. Shima sai ya zuba mata nasa kawai yana kallonta cike da shauƙi. Cikin motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Ke ƙyaƙyƙyawa ce Mawaddatan’warahmah”.
Da sauri ta buɗe idanun nata a daburce, dan yanda ya furta kalmar sai taji kamar ya haɗa da jinin jikinta ne ya zuƙe har ma da numfashi, kafin ta samu damar cewa komai Usman yay sallama. Amsa masa yay yana mai dafe goshinsa da faɗin, “Gaskiya baka iya zuwa ba”.
Ƙaramar dariya Lulu tai tana kauda kai, shi kuma ya harareta da bashi izinin shigowa bayan ya miƙa mata mayafin da ke ajiye gefenta da faɗin, “ALLAH yasa ma ba haka kike zama min a gabansa ba yana kallemin kayana”. Yanda yay maganar cikin ɓata fuska ya sakata sake sakin murmushi, cike da neman tunzurashi ta ce, “Mi kuma ya rage bayan shine mai karɓar haih….”
“Mtsoww! Shut up!”.
Ya faɗa a hasale yana balla mata harara fuska a gimtse. Dai-dai nan Usman ɗin ya ƙarasa shigowa, sama-sama ya bashi hannu suka gaisa, kafin ya ɗan juya yama Lulu tambayoyi game da yanayin jikinta. Ta tabbatar masa da Alhmdllh bata jin komai. Shima hamdalar yay yana ɗan duban Smart da murmushi, “Oga zamu iya wucewa masauki ko anan zaka kwana ka taya Madam jego? Dan itama lokacin barcinta yayi”.
“Kaga dana ɓarke ɗinkin sai ku tara min jama’arku na likitoci kenan”. Smart ya bashi amsa da ɗan barkwanci duk da da gaske maganar Lulu ta sosa masa zuciya amma ya danne.
Ƙaramar dariya Usman yay da faɗin, “Ai kai oga ne zamu ɗaga maka ƙafa kodan Son ɗina AA”.
Murmushi Smart ya sake yi kawai bai ce komai ba. Usman kuma ya matsa ga Lulu ya mata allura da duk sauran abinda ya dace sukai mata sallama, gaba Usman yay ya barsa. Ganin yanda Smart ɗin ya raka bayansa da kallo mai kama da harara yasa Lulu saurin faɗin, “Nifa wasa nake maka kada ka ƙullacin bawan ALLAH bayan ƙoƙarin sa a kammu. Kana dai ganin a yanda yay min allura ma cike da taka tsantsan”.
Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da ɗan lumshe idanunsa da launinsu har ya canja. Batare da yace mata komai ba a karo na biyu ya ƙarasa gareta ya rungumeta tsam-tsam a jikinsa ta yanda dai bai taɓa mata ciwo ba. Su dukansu babu wanda bai sauke ajiyar zuciya ba, yayinda Smart ya shiga laluben lips nata. Da sauri ta janye jikinta saboda jiyo takun tahowa, shima sai ya miƙe dan dai-dai nan Ammah tai sallama. Gaban gadon Babyn ya koma tare da kama hannayensa ya fara tofa masa addu’oi. Har saida ya kammala sannan ya ɗago yana kallon Ammah da ke taimakawa Lulu ta kwanta yanda zataji daɗi. Sun ƙara haɗa ido da Lulun ta kauda kai shima ya kauda da ɗan salon taɓe baki yana wani lumshe idanunsa…..
*_NIGERIA_*
Sosai jikin Dada ya ruɗe a safiyar yau dan haka hankalin ƴaƴanta a tashe yake matuƙa. Cikin ƙanƙanin lokaci aka shirya mata barin ƙasar. Baba Garko na Abuja a lokacin Uncle Khamil ya kira shi a ruɗe yana sanar masa zai tafi Kano jikin Dada ya tashi sosai. Duk da ya ji damuwa a ransa sai ya danne cikin nuna halin ko’in kula ya ce, “ALLAH ya bata lafiya” ya kashe wayar abinsa. Abinda Baban yay ya sake tada hankalin yaran. Dan sun sake tabbatar da har yanzu ransa a ɓace yake akan mahaifiyar tasu. Haka suka shirya wasu a cikinsu suka wuce da ita gwiwa a sage. Wanda aka bari a gida kuma suka bita da addu’a kafin suma subi bayansu da ga baya. Matansu kam addu’a suke ALLAH yasa da ga can ta wuce ko zasu huta da samun sukunin zama da mazajensu cikin ƴanci kamar kowacce mace a gidan aurenta. Dan gaskiya surukar tasu ta musu kane-kane a cikin rayuwar aurarrakin nasu….
(To mudai munce ALLAH ya baki lafiya Dadansy).
__________★
Duk da zuciyarta a dagule take da wannan tafiya ta mijinta da kishiyarta da tafi tsana fiye da kowa a rayuwarta ta wani fannin hakan ya taimaketa, dan ta samu damar aiwatar da mugayen nufinta akan wanda suke wa taƙamar da tinƙaho. Saboda tayi alƙawarin kofa komanta zai ƙare ita sai taga bayan Smart da uwarsa. A haka ma dan bata san ainahin abinda ya kaisu UK ɗin ba kenan. Hankalin aunty amarya ya tashi da ganin kai-kawon da Umma ke yi, dan haka kawai zuciyarta ke ayyana mata kai-kawon bana banza bane ba. Su dukansu sun jima suna zargin Umma akan shige-shigen gidajen malamai. Dan a wasu lokutan sukan kasa gane kan mijin nasu ta koma sai ita kaɗai ce madubin dubawarsa. Sai sun dage da addu’a abin yay sauƙi kafin ta sake masa sabon aike. Wannan dalilin yasa a yanzu ɗin ma Aunty Amarya ta shiga damuwa. Sai dai ta rasa dawa zatayi maganar dan Mama ita ba gane kanta ake ba wasu lokutan sai a hankali ce. Ga shi su Maryam basa nan. Ganin abin nata cigaba da alamomi masu yawa ta ɗaga waya tai kiran aunty Bilkisu akan tazo dan ALLAH idan ta samu lokaci. Da sauri Aunty Bilkisu ta tabbatar mata da gatanan zuwa.
Da yamma ko sai gata, sai dai ta nuna kamar daga wani waje take ta biyo gaishesu. Sama-sama Mama da Umma suka amsa mata gaisuwarta, dan suna cike da takaici da kishin tafiyar Abba da Ammah. Aunty Bilkisu bata nuna ta damu ba ta shiga ɗakin aunty Amarya abinta. Tsakanin aunty Bilkisu da aunty Amarya suna abune kamar ƙawaye, duk da aunty Bilkisun ta girmeta kaɗan, bayan sun gaisa babu ɓata lokaci suka shiga tattauna abinda ya tara su. Sosai hankalin Aunty Bilkisu ya tashi da bayanin aunty Amarya, duk sai ta rikice. Cikin kwantar da hankali aunty amarya ta ce, “Bilkisu dan ALLAH karki ruɗa kanki, mu nutsu muyi tunanin abinda ya dace, dan kinga dai bawai tabbas garemu ba zargi ne”.
“Aunty wannan ai ya wuce zargi tunda har kinji tana ambatar sunan Hydar ɗin da matarsa. Wlhy nikam al’amarin Umma ya fara bani tsoro a gidan nan. Ko kin san kwanan nan sai da taje ta kaima kishiyata gulmar Ammah da har ta kaimu da yin faɗa. Alhaji ne ya tausheni da kar nazo gida na faɗa kamar zaimin kuka. Kuma ya tabbatar min da ai ta daɗe tana kai musu gwabsona dana Ammah kawai dai yanzu ne ALLAH ya tona asirinta. Akan wannan rigimar yanzu haka uwargidana na gidansu ya mata saki ɗaya”.
“Innalillahi. Itako Umman Hannatu mi take son zama ne? Wlhy al’amarin ta na bani mamaki”.
“Dolene abinta yake bada mamaki ai Aunty, ki duba fa yanda ta tada hankalinta a gidan nan tunda taji Hydar na ƙasar waje. Ni wlhy zuciyata ma har ta fara zarginta akan matsalar da yayta samun nan a baya. Kawai dai dan Ammah tace kar nayi magana ne”.
“Eh ai tabakin Yayar gara a barta, ita da kanta halinta zai tsangwameta kowa ya shaida. Amma yanzu idan akaji a bakin wani a cikinmu za’a ɗauka sharrin kishi ne kawai. Kin san kuma Yaya ita komai nata a nutse ne bata son gaggawa. Shiyyasa yanzu ma kikaga na nemoki dan kota dawo bana son na fara mata maganar, duk da nasan zata fahimce ni”.
“Hakane Aunty, yanzu to yaya zamuyi?”.
“Addu’a zamu dage da ita, mu kuma saka a cigaba dama Aliyu shima har sanda su Yaya zasu dawo miji nata shawaran”.
Aunty Bilkisu ta gamsu da shawaran aunty Amaryan, dan haka suka cigaba da tattaunawa. Bata bar gidan ba sai bayan sallar magrib……..✍️
_Network kaje dan kanka. Na barka da ƙarfen da ake maƙalaka ehe🥱🥱🚴_.
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣6️⃣
…….Kamar yanda Daddy ya faɗi zasu tattauna da Smart tun a waya ya cika alkawari, dan washe gari tunda safe ya baro Abba da Uncle Yousuf ya sami Smart a gidan su Usman dan nan ya kawoshi. Sun gaisa cikin mutunta juna kafin su fara tattaunawa. A nutse Daddy ya fara ma Smart bayanin mafarin komai tsakaninsa da Sulaiman har zuwa yau da suke tare. Matuƙar girgiza Smart ya shiga, tare da jinjina ƙarfin halin Daddy da sake ganin kimarsa. Ya jure ɗaci da damuwa saboda kawai karya rama sharri da alkairi, saboda kare mutunci da lafiyar ahalinsa. Cikin zubda hawaye Daddy ya katse Smart da faɗin, “Abu ɗaya ne ke cimun zuciya a yanzu Aliyu shine cutar da matarka da nayi, kwarai da gaske na zalunci rayuwar Mawaddat dan rashin ilimin addini babbar naƙasu a rayuwar ɗan adam. Gara ace mutum bai san komai a limin boko ba dan wannan iya kar alfaharinka da shi shine duniya. Inajin kunyarta ta yanda a duk sanda na tunata nakanji hawaye na zubarmin tunda ba haka naima sauran ƴan uwanta ba. Wlhy alokacin idanuna ne suka rufe da iya tunanin kuɓutar da ita da ga sharrin Sulaiman ne kawai shiyyasa. Iya ƙoƙari Yousuf kuma yayi na ganin ta samu ilimin har malami ya nema mata a can Germany amma tsoron karda a haɗa baki da Malamin a cuta mata yasa na hana hakan. Ashe na manta UBANGIJI shine mai ikon tsarewa da killace bawa da ga sharrin masu makirci da ƙulle-ƙulle ba wai wayo ba. Domin nayi gudun gara na faɗa gidan zago. Dan ALLAH ka tayani bata haƙuri da neman gafararta, ka tayani gina mata sabuwar rayuwa, ka tayani horas da ita sababbin ɗabi’u, ka tayani ɗorata a hanyar tsira Aliyu kafin ɗan sauran lokacin da ya rage min ya ƙure mana ni da ita. Dan nasan da wahala na tsallake da ga tarkon Sulaiman saboda shu’umi ne na gaske. A yanzu haka ya ƙullaci mahaifinka akan maganar kotun nan, amma Alhamdullah babu abinda ya isa masa dan duk inda ya saka ƙafa na saka ƴan sandan farin kaya biye da shi, bama shi ba hatta ƙannenka dake gida dana ma’auri al’amarinsu na ƙarƙashin kulawar hukuma a duk sanda zasu bar gida. Kayi haƙuri kaima Aliyu na sakaka a rigimar da baku san mafarinta ba, shiyyasa raina fansa akan ganin wani abu bai cutar da ku ba a dalilina. Amma dan ALLAH ku yafe min duk laifina ne, da ace nayi nazari kafin na biyema Sulaiman tun farko maybe da duk bamu kai a irin wannan matakin ba…..”
“Daddy jarabawace kawai, bawa kuma bai isa tsallake ƙaddararsa ba. Ba kamana laifin komai ba sai alkairi a rayuwa. Babu abinda zan iya cemaka sai godiya da cigaba da maka addu’a har ƙarshen numfashina. Ba laifinka bane Mutumin nan hatsabibin ne na gaske. Na fahimci hakan tun a haɗuwata da shi ta farko. Dan haka na zauna na karancesa yanda ya kamata, sai dai rashin sanin abinda ke a tsakaninku yasa ban taɓa wani yunƙuri ba. Amma tabbas na jima da lura da duk inda nake ana biye da ni, hakama ƙannena, na shiga tashin hankali saboda a tunanina Sulaiman ne, sai daga baya na fahimci ƴan sanda ne, sai dai babu irin bibiyar da ban musu ba sunƙi gayamin wanda ya sakasu, sai nai tunanin ma ko Uncle Yousuf ne ko Coach a lokacin, shiyyasa na zaɓi musu shiru a ganina wataran ai zan sani. Kamar yanda na faɗa maka ina son ka bar wannan case ɗin a hannuna yanzu, sannan ina son na bada shawara….”
Cike da kulawa Daddy ya ce, “Ina jinka Aliyu, ka faɗi komi ke’a ranka kai tsaye tsakaninmu babu wani ɓoye-ɓoye”.
Kai Smart ya jinjina tare da furzar da iska mai nauyi. “Wato Daddy irin su Sulaiman da hatsabibancinsu yaƙin sunƙuru yake buƙata a farkon fara wasa. Kamar yanda ka ɗauki masa salon shekarun da suka gabata na nuna baka san mi yake ciki ba wannan salon zamu cigaba a yanzu har zuwa wani mataki. Domin idan har akace za’ai masa fito-na-fito a shirye yake da wannan tun ba yanzu ba. Jirace yake da kai kace kule yace cass. Sannan mahaifinsa da kai hallacin shanye komai daminsa zai iya samun bugawar zuciya wlhy in har yaji kasuwancin da yake yi da kuma ketama autarsu mutunci da yayi. Ko kuma shi da kansa ya shirya hanyar halakasu idan yaga zaka cimma burin tona masa asiri. Kaga anyi gudun gara kenan an faɗa gidan zagon dai. Dan haka mu ajiye batun fito-na-fito ɗin nan mu lallaɓa Baba Garko ya sakar masa ɗansa, ka cigaba da nuna masa kana shakkar tasa, sauran yaƙin ka bar mana zamu ƙarasashi ni da Mawaddat da Uncle Yousuf in sha ALLAHU”.
Idanu kawai Daddy ya zubama Smart, yama rasa abin faɗa akan wannan yaro. Lallai farar haihuwa tayi, dan shikam dole ya kira wannan yaro da farar haihuwa ga iyayensa. Smart ne da yaga kallon da Daddyn ke masa yay ƙasa da kansa yana murmushi kawai….
__________★
Yau kam Ammah da kanta ta wanke ɗan jikanta ta gyarashi ɗaras ɗas. Yayinda Mamy ta gyara Mawaddat ita kuma Ummita ta shirya abinci. Lulu da ke jin jikinta wani iri tunda garin ALLAH ya waye cikin damuwa take sanarma Ammah ta mata addu’a gabanta sai faɗuwa yake. Jawo hannunta Ammah tai ta zaunar kusa da ita cikin damuwa da kulawa ta fara mata addu’oi, a hankali Lulu ta dinga samun nutsuwa har ta ɗan sha tea ta kuma shayar da AA abincinsa. Sun kammala kenan Ummita na gyara mata gashinta su Smart suka iso niƙi-niƙi da kayan da ya siyo bisa jagorancin Usman. Da mamaki Lulu ke kallonsu su da kayan, Usman ya nuna Smart cikin ɗaga hannu yana ficewa acewarsa bari yay kiran Dr Lameer.
Lulu da ke jin faɗuwar gabanta na dawowa tun shigowar Smart ɗin ɗakin cikin dauriya ta ce, “Good morning” a takaice. Bai amsa mata ba sai da ya ɗauki AA tare da kaiwa zaune cikin kujerar dake a gaban gadon ya ɗan ma yaron kiss a goshi da kumatunsa sannan ya dubeta idanu ƙasa-ƙasa. Kamar wanda baya son motsa lips ɗinsa ya furta, “Haka ake gaishe da miji? Kamata yay kizo da gudu ki rungumeni da bani ƙyaƙyƙyawar sumba ki ce good morning rabin raina” yay maganar cikin kwaikwayon muryarta. Harara ta zuba masa da saurin faɗin, “ALLAH ya kiyasheni. Miye wani rabin rai babu ko daɗin ji…..”
“Ki rantse ni ba rabin ranki bane”.
“Kana buƙatar ganin likita kam”.
Murmushi ya saki da ɗan lumshe idanunsa yana gyara AA da ƙyau. “To muje a hakan, idan tai wari maji ai. Ina fatan kun tashi lafiya ke da baban Ammah?”.
Cikin ɗan marairaice fuska ta ce, “Wane lafiya bayan ya hanamu barci, ka masa faɗa gaskiya ni bana son damuwa. ALLAH nima sai da nai kuka duk ya ruɗamu ga Ammah tayi tafiya ta gaji ya sata tanata faman jijjigarsa”.
Gaba ɗaya neman harmutsa masa lissafi take da salon nata. Ƙaramin gyaran murya yay saboda jin yawu na neman sarƙeshi. Hakan yasa Lulu zuba masa ido, sai yay saurin janye nasa da ke neman canja launi cike da basarwa ya ɗan lakace kumatun AA da faɗin, “My Grandpa miyasa ka hanamin Mata barci? To da ga yau karna sake ji kaji Sadaukina. Kuma ka bama Maah-maah haƙuri” Sai kuma ya ɗago ya dubi Lulu data zuba musu ido, a yanayin ɗan ɗage gira ya ce, “Koda yake ni ya kamata ma na bada haƙurin nan a madadinsa” ya ƙare maganar yana tasowa. Ƙoƙarin sauka tai a gadon tana faɗin, “Ni dai ban gayyaceku ba”.
Cikin ɗan murmushi ya ce, “Oh oh har ma takai gudunmu akeyi. Haƙuri da kawai zamu baki”.
“Na haƙura basai kunzo ba”.
“Please mana Baby luv ko ɗuminki ki bari muji mana”.
Dama ta fahimci wayon nasa kenan, dan haka ta maƙe kafaɗa kamar wata ƴar baby da faɗin, “Naƙi ɗin. Kai koma kunya bakaji a gaban ɗanka sai kayi taɓara. Ka rage halin nan wlhy rashin jin magana zalla”.
Komawa yay ya zauna yana dariya da faɗin, “Kema ai rashin jin ne ya kaiki ga samo AA Mawashi. Haka kawai kin lalatama Ammah yaro, sai kawai ta ganki da yaro a hannu kuma dai tasan a inda kika samo…..”
“What!!”
Ta faɗa da sauri cikin daburcewa kamar Ammah na gabanta. Aiko ya shiga yin dariya a hankali. “Ni dai ai kowa yasan ni babu ruwana salihin ALLAH. Ina zaman zamana kikace sai anyi yaƙin ƙasa da ƙasa. Tsabar zalama baki fito a filin dagar ba sai da ganimar yaƙi wannan yarinya sai a barki kawai amma dai gaskiy….”
Fillon data ɗauka zata jefa masa ya hanashi ƙarasawa, cikin ɗaga hannaye sama da sauri alamar surrender ya ce, “Yi hakuri nayi shiru, ke kam akwai kawaici nine zalamammen ga shi ma AA ni yabiyo tabbacin haka”.
Hararsa tai da ajiye filon ta koma ta zauna. Sai kuma cikin damuwa da marairaicewa ta ce, “Da gaske dan ALLAH su Ammah suna ganin bani da kunya ko? Wata goma da kwanaki dayin aure na haifi yaro, wlhy nima abin na damuna, sai nake ganin abin yayi kusa da yawa kamar wata mayyar miji”.
Daƙyar Smart ya iya danne dariyarsa. Dan ya fahimci tsakaninta da ALLAH take tambayar. Cikin kaɗa kai ya ce, “Kai kai baza’a suce ba Madam. Sai dai ma a kiraki da jaruma mai matuƙar hazaƙar ɗaukar darasi a wajen malaminta. Ammah kam ai zata so nan da wasu watannin goma masu zuwa ki sake santalo mata wata baby girl ma again”.
Sosai ta waro manyan idanunta kamar zatai kuka. “Hydar wane fatan tsiyane kuma wannan dan ALLAH mutum ko gama dawowa hayyacinsa baiyi ba kamar wata akuya. Kasan miye rainon ciki da haihuwa kuwa?. Wlhy akwai wahala, ni da ga ɗayan nan ma na gama gaskiya”.
Tsam ya taso da ga inda yake zaune ya dawo kusa da ita. Cikin nuna damuwa ya ce, “Da gaske akwai wahala? Bani labari yaya kika kasance?”.
Lumshe idanunta tai a hankali tana mai ƙara shaƙar ƙamshinsa mai masifar daɗi, duk da dama dai tun ɗazun take shaƙar, kusancin da suka samu yanzu ne ya ƙara ƙarfinsa sosai a cikin han nacinta. Hannunta ya ruƙo tare da murzashi a cikin nasa a hankali. Idanun ta buɗe tsigar jikinta na tashi. Ta kalli hannayen nasu ta ɗan sake lumshe idanun nata da sake buɗewa. Cikin ƙara ƙasa da muryarta batare da ta farga da canja salon harshen nata ba ta furta, “Ai ya wuce kuma, share kawai”.
“Please ina son ji nidai”.
Ya faɗa yana murza mata hannu a ɗan marairaice. Hannun taso janyewa dan yana sata a wani yanayi salon nasa, amma ya hana hakan, sai kawai ta saki ajiyar zuciya a hankali ta furta,……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣7️⃣
…….“Humm akwai wahala sosai da bata da misali. Na ƙara jin ƙaunar mahaifiyata da jinjina mata wahalar da tai dani a dalilin wannan cikin. Ko abinci bana iya ci, da naci sai amai, ko wani abu na sha sai nayi amai. Gashi nan ko yanzu dana haihu magani ma ya gagareni sai dai allurai ake min dan in naga magani amai nake ji. Kunun gyaɗa ne kawai ya zama abincina kwana da yini. Gaba ɗaya dai abin babu sauƙi kawai dan ba’a iya misaltashi ma Aliyu. Balle naƙuda Hummm……”
Duk da a dunƙule ta bashi labarin ya fahimci dai ciki ya hanata shaye-shaye, sai kunun gyaɗa daya zamar mata abinci kawai. Cikin ƙara sanyaya murya da jin tausayinta da farin ciki ya ce, “Addu’ata dare da rana UBANGIJI ya tasirantar da itane atare da gudan jinina, ya ƙarasa min aikin dana fara kenan, sannan a kowane awa bayan awa yana tuna miki Abbiensa ne ta hanyar shan abinda yafi so fiye da komai.” yanda ya ƙare maganar da ƴar dariyar tsokana ya sata ɗan harararsa da taɓe baki, sai dai batasan hararar tata ba ta juye ne zuwa wani sassanyan kallon dake neman hargitsama Smart lissafi da hankali.
“Ita hararar nan tana son tada zaune tsaye ne fa. Zakuma ta iya takalo yaƙin ƙasa da ƙasa a taƙaice rigakafi yafi magani”. Ya faɗa a wani irin kasalance yana ƙasa-ƙasa da idanu. Ba fahimtar zancensa tai ba, amma salon da yay maganar da yanda yake wani narke idanu da murya ya sata janye jikinta a nasa cikin basarwa duk da saƙon nasa ya isa ga manyan mata fiye da yanda yay tsammani. Shima kawai sai ya basar cikin sauke ajiyar zuciya ya ce, “Yanzu miye shirinki akan suna gobe idan ALLAH ya kaimu?”.
Cikin mamaki ta ce, “Suna kuma? Da suwa za’ayi sunan to? Bayan naga idan za’ai suna a gida Nigeria taruwa dangi sukeyi da matan anguwa, in dai ban manta ba haka na gani a sunan Deen ɗin mu fa anyi, anan kuma mu yanzu wa garemu da zai zo?”.
“Mu mana, iya mu ɗin nan ma ai mun wadatar muyi suna bawai wajibi bane sai antarun kamar yanda kika gani a sunan Deen, in sha ALLAHU kuma za’a yanka masa rago kamar yanda ake yankama kowa. Ƙyautar da ban san da itaba ce ba fa a hannuna, taya bazan nuna godiyar ALLAH ba nikam. Sannan ni so nake daga nan mu wuce kawai basai kin koma Nigeria ba”.
“Hanyoyin nuna godiyar ALLAH ai suna da yawa ba sai ta hanyar yin taron suna ba. Sannan idan ban koma Nigeria ba ina kake son naje banda neman magana irin taka. Kuma ni nama faɗa maka na shirya cigaba da zama da kai ne? Auren contract akayi kuma ya ƙare it’s ok”.
“Hakane kam, Alhamdullah suma waɗan can godiyar UBANGIJI ɗin duk na kamanta su, amma duk da haka dai ina son muyi shagalin suna. Kinga koda ƙannensa sun zo nan gaba suma shi bazaiga an musu ba’ai masa ba”. Ya ƙare maganar batare daya amsa maganartata ta ƙarshe ba.
Hakan ya bata haushi, dan haka a tunzire ta ce, “Miye wani ƙanne? Malam ka san abinda kake faɗa fa! Na gaya maka ni na gama auren nan”.
Dariya ta bashi ganin yanda tai maganar a gatsire, amma sai ya danne da ƙyar yay murmushi kawai da faɗin, “Naki tsarin kenan wannan ai”.
“Kamar ya nawa tsarin kenan?. Amma kasan dai ba haka akai da kai ba ko?”.
“Humm” yace kawai. Baice komai ba akan maganar tata yanzun ma, sai ma ya nuna mata ledojin da suka shigo da shi. “Kuyi haƙuri da waɗan nan babu yawa, sauran abinda ya dace duk na damƙashi a hannun Usman. Munyi magana da Daddy akan suna son a turaki Saudiya ki zauna a can na wani lokaci saboda Kawunki Sulaiman, dan bazai taɓa ƙyaleki ba zai cigaba da bibiyar al’amarin ku. Ke yaya kika gani?”.
“Ni babu inda zani, shi ɗin banza da zan cigaba da masa wasan ɓuya. Ko wannan ɗin ma da yaga yaci nasara saboda Dada ne wlhy, sannan ina kan sani na cigaba da biye masa bayan nasan manufarsa. Nayi hakkanne kawai domin sake tabbatar da shi ɗin waye. Amma har miye wani Sulaiman can”.
Murmushi yayi kaɗan, a zuciyarsa yana ayyana (ashe a wajen Daddy kika gado wannan taurin ran naki da kafiya) a zahiri kam sai ya nisa cikin ɗan cije lips ɗinsa ya ce, “Zamu iya tunanin shi ba abin tsoro bane ba, sai dai idan muka shagala da hakan zai mana illa a ƙanƙanin lokaci cikin salon duka ta inda bazamu taɓa iya sosawa ba balle mu rama. Mawaddat Kawunki ya wuce duk yanda kike tunani a kansa. Domin ya jima biye da rayuwarki tun kina ƙarama. Bana raba ɗayan biyu shine ya koya miki shaye-shaye. Kuma shine ya taɓa harar rayuwarki ta hanyar keta miki haddinki har kike firgita kika tsani maza….”
Da wani irin sauri ta kallesa, sai kuma jikinta ya fara tsuma. Dan danan annurin fuskarta ya ɓace gaba ɗaya. Cikin yanayin faɗa-faɗa ta ce, “Aliyu rayuwata ta baya ta zamar maka abar bibiyane ko mi?”.
“No ko ɗaya, mizai sa na bibiya bayan na gama fahimtar komai. Sannan Mawaddat nake so ba halayenta ba. Ruwana ne na maidata a irin halayyar da nafi buƙata kona barta da wanda na ganta a ciki. Mawaddat ki sani shure-shure baya hana mutuwa, duk yanda kike jin zaki iya ɓoye abinda ya faru a baya wataran zuciyarki bazata iya ɗauka ba. Kiyi haƙuri ba ina tilasta miki bane sai kin sanar min, kidai sani cigaba da riƙewar zai iya sake nakasaki akan shaye-shayen nan. Doctor ya jima da tabbatar da idan kika cigaba zaki cutu, sannan a yanzu ke ɗin Uwa ce Mawaddat, taya kike tunanin idan yaron mu ya taso yaji wannan ɗibi’ar koda a labari ne zaiyi farin ciki. Mahaifiyarki mutuniyar kirkice data shinfiɗama rayuwarta alkairai da dama da a yanzu sune ke bibiyarta da ke kanki har maƙiyanki da nata suka gagara cin galaba a kanki. Taya kike tunanin naki ɗiyan zasu samu irin wannan kariyar idan har baki zama uwa ta ƙwarai ba Mawaddat. Please ina so ki canja, canjawar taki kuma zata tabbatane kawai ta hanyar fidda abinda ke zuciyarki, dan shine yay miki nauyin da har kike jin abinda kike sha zai iya danne miki shi. Taya za’a gyara ɓarna da ɓarna banda wautarki……”
Wani irin kuka mai tsuma zuciyar da ta saki ne ya saka shi yin shiru, a hankali ya furzar da iska tare da miƙewa ya koma daf da ita, matsota yay ya saka a jikinsa ya rungume. Sai kawai ta sake sakin masa kuka da iya dukkan ƙarfinta da baƙin cikin dake cinkushe da zuciyarta da ƙwaƙwalwa. Bai sake mata magana ba ya barta tai kukan mai isarta dan haka zai rage mata nauyin zuciyar. Tako yi kukan sosai dan sun kai kusan awa guda tana abu ɗaya har sai da taji kanta na sara mata sannan tai shiru ta koma shashsheka. Cikin son kauda yanayin ya ce, “Uhm nace ba! Yau dai anan zan kwana ko? Naga ai gadon zai ishemu”.
Da sauri ta ɗago tare zuba masa harara da kumburarrun idanunta da suka sha kuka. Murmushi yayi da marairaice face yana shafa kai. “Nifa bance wani abu ba Madam. A wajen kwanciyar ma na yarda sai ayi kai da ƙafa AA a tsakkiyar mu. Kinga dai ai babu batun kawo harima balle ace da wata manufa nazo”.
Filo ta ɗauka ta maka masa. Ya shiga karewa shi kuma yana ƙyalkyala dariya. Dai-dai nan Usman yay sallama. Hararar ƙofar Smart yayi cikin dafe kai. Hakan ya saka Lulu dariya ta amsa da cema Usman bismillah shigo. Babu kunya yana shigowa Smart ya hararesa da faɗin, “Kai wai miyasa baka iya zaɓar lokacin zuwa bane ɗakin mutane?”.
“Oh ba’ai farin ciki da zuwana ba kenan na koma?”.
“Eh gaskiya koma anjima sai ka dawo, wannan ai shiga tsakanin masoya ne”.
Ita Lulu abin harya bata kunya tana kallon Smart ɗin a daburce, sai taji Usman ɗin cikin dariya yana faɗin, “To kama jama kanka yanzu ma anan ɗakin zan koma yini”.
“Uhm saboda ka sake tabbatarma da duniya kai ɗan Sa ido ne kenan?. To aiko addu’ar tsole ido zan fara da tsiyaye ido, ba sai naga da idon da zakai sa ido ba”.
Cikin mamakin yanda suka saki jiki da juna a ƙanƙanin lokaci bayan tasan Smart da shegen ɗaukar kai wa mutane ta ce, “Wai dama kun san juna ne kafin jiya kenan ko me?”.
Dariya Usman yayi, yayinda Smart ke murmushi yana harararsa. Cikin marairaice murya ya ce, “Inafa ya sanni Baby luv. Jiya fa daya rabani da ke a ɗakin nan ya tafi dani can ya dinga isa ta da surutu kamar rediyo. Har sai da ya nema sakamin ciwon kai”.
“Kinga laifina ne Momyn AA. Ni ban iya kurumta ba, naga ana neman maidani kurman ƙarfi da yaji bayan ga ɗan ƙasata na gani. Ni mamaki ma nake yanda yake miki hira ke ko mu ya raina kenan dai yake mana shiru-shiru”.
Murmushi Lulu tai da kallon Smart ɗin, dan tasan zaman Usman a ɗakin nan da saka musu baki da take dauriya kawai yake yi. Ita bata taɓa ganin mutum mai kishin tsiya irinsa ba kodan bata rayu a Nigeria ɗin bane oho. Ilai kuwa kafin ta gama tunanin nata ya miƙe tare da jan hannun Usman ɗin ya na faɗin, “Muje tunda dai ka rantse sai ka rabamu sa’ido master”. Da ga haka yaja hannun Usman suka bar ɗakin.
Ajiyar zuciya Lulu ta sauke da maida kallonta kan AA bayan ficewarsu da ganin Hararar da Smart yay mata sanda yake ficewa. A dai-dai nan Ummita ta shigo ɗakin da sallama. Harara Lulu ta sakar mata cikin wasa da faɗin, “Sai yanzu ake ganinki? Ɗan naki ma yayi fushi ai shima”.
“Oh oh karki haɗamu faɗa Aunty, my sweetheart, I’m sorry sorry naga kana tare da Daddy ai yau ko shiyyasa ban zo ba” Ummita tai maganar tana ɗaukar AA da manna masa kiss a goshi. Har zuciyarta take jin ƙaunar yaron, dan ya shigar mata rai sosai. Murmushi Lulu keyi, sai kuma takai kwance da faɗin, “Su Ammah barci sukeyi ne?”..
“A’a suna hira abinsu tun ɗazun. Amma gasu can tare da su Daddyn AA yanzu suna magana. Ashe gobe idan ALLAH ya kaimu shagalin sunan Yarona zamu sha?”.
“Ku kuma ƴan son bidi’a dama haka kuke so ko?”
Dariya Ummita tayi ranta fes……✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣8️⃣
_________________
…….Har dare Lulu bata sake saka Smart a idonta ba. Suna can sunyi busy shi da su Usman. Sai ma zuwa yamma ne da kewarta ya ishesa ya sa Usman yay masa kiranta a wayar Mamy duk da tsiyar da yeke masa bai kulashi ba. Gaisuwa kwai sukai a wayar ya tambayi AA tana amsa masa cikin basarwar nan tata. Gajeren Murmushi kawai yayi da jinjina jan aji da son tsare girma irin na Lulu. Ya jima baiga mace mai ɗankaren basar da abu ba irinta. Shi kaɗai yake iya gane wacece matar tasa, shiyyasa yake sarrafata a salon da takan zurma ta saki masa jiki batare da ita kanta tana sanin ta zurma ɗin ba. Dan ita Lulu zuma ce, idan kace ma zaka bita da wutar maimakon cin nasara kai wutar zata dawo ta baibaiye ne. Shiyyasa yake amsar zaƙin nata da harbin duka gaba ɗaya sannan ya bita da feshin furanni masu ƙamshi…
Lulu tayi mamakin ganin irin ƙwarya-ƙwaryar liyafar da aka shirya cikin ƙanƙanin lokaci nan. Ba ita ba hatta su Ammah sunyi mamakin hakan. Sai dai Ammah taji daɗi sosai. Har dare suna abu guda. Bayan sun nitsa ɗin domin su huta ɗin ma gajiya ta hanasu zama a gidan. Lokacin da ya shigo ɗakin musu sai da safe Lulu ma tayi barci saboda alluran da ake mata. Yaronsa kawai yay ma addu’oi da kiss, idon Ammah kuma ya katangesa ga zuwa inda Lulun take sai dai kallo da ga nesa.
Washe garin cikar sati guda da haihuwar AA suka wayi gari da shagalinsu da kuma isowar Ahmad da Coach, dan Smart yace idan zai iya ɓoyema kowa banda mutanen nan biyu. Yaro yasha addu’a a wajen Coach da Ahmad, Lulu da Smart kuma sun sha sheri wajen Ahmad dan sai da Lulu ta koma ɓoyewa idan taji maganarsa. Duk da bawani yawane da su ba abin dolene ya ƙayatar da mai kallo. Kamar yanda Smart ya faɗa an yankama AA ƙaton ragon turawa, a take kuma aka gashe shi gashi mai ƙyau da tsafta ya shiga jerin abinda za’aci a wajen shagalin. Duk da Lulu na dojewa haka dai dole ta shirya a cikin kayan da Mammy ta kawo mata sabuwar doguwar rigar shadda babba sosai da bazata takura mata ba saboda ciwonta. A kallo ɗaya mai kallo zai san shaddar taja kuɗi, maiƙon da take ma kawai da stones work da aka zuba mata na azaba abin ba’a magana. Bawai an ɗinka kayan bane dan wannan taron, kayan Mamy ne ta ɗinka abinta sai dai bata taɓa sakawa ba. Tunda wannan ta taso sai kawai ta ce Lulu tai amfani da su. Karo na farko Lulu tasa kayan da ba fitet ba a jikinta. Amma sai tai ƙyau sosai musamman da Ummita ta mata ɗauri mai ƙyau sosai, ƙanwar Usman da sai yau suka fara ganinta tai mata kwalliya tana dojewa ta na komai sai da akayi. AA ma an shiryashi cikin wasu tsadaddun kayan yara masu taushi da ƙayatarwa da Abbiensa ya siya masa. Angon jego ma yayi nasa ƙyawun cikin lallausan farin yadi da ya zauna masa ɗas ya fito a cikakken bahaushen sa ɗan Nigeria dan harda hula. Ita kanta Lulu a kallo ɗaya data masa ta sake tabbatar da jiya fa ba yau bace, ƴan maza sun gama cika mazaje sai dai fatan tsahon rai kawai da gamawa da iyaye lafiya. Yanda yake satar kallonta haka take satar kallonsa. Sai dai in sun kama juna ta hararesa ta basar. Yakanyi murmushi ya ɗauke kansa kawai. A haka dai aka fara ɗan taron da iyakar sune sai Dr Lameer da iyalinsa da ƙanwar Usman da boy friend ɗinta data gayyato. Sai abokan Usman biyu da suna ganin Smart suka shaida shi kasancewar su masoya ƙwallo, sun kuma bibiyi wasan link na ƙasar England. Ɗaya ma ɗan can ƙasar ɗinne. Lulu dai tayi mamakin a ina suka kwasosu? Da yanda suke girmama Smart ɗin da wani tattalinsa duk ya ɗaure kanta dan kowa dai yasan waye bature. Sai dai batace komai ba dai ta bar abinta a zuciya tana taɓe baki. Gaba ɗaya taron nasu dai basu fi su ashirin ba. An kuma yisa cike da birgewa da ƙayatarwa, gashi babu wata hayaniya sai ɗan cool music da aka saka na waƙoƙin masoya, duk da dai Ahmad ya saka waƙar data shiga har cikin jini da ɓargon Lulu da Smart ta hausa. Wato (Labarina baya zama nawa ta Salim Smart da KEWA ta Auta Waziri). Amma da farko basu saka ba saboda su Abbah. Sai da sukai addu’oi wa jariri da mai jego dama uban jego sannan. Can cikin lambun Abbah da Daddy da mahaifin Usman suka koma abinsu suka baje suna hirarsu ta dattijai da tarin abinci da aka shirya musu. Yayinda Ahmad da Usman da hali yazo ɗaya a rawar kai suka warware sautin sai dai bamai hayaniya ba. Ansha hotuna kala da iri, sai dai a duk sanda za’ai Smart na naniƙe da Lulu, idan da namiji za’ai tana gefensa ta inda babu kowa bai yarda wani ya raɓar masa mata ba. Tunma su Usman basu farga ba har suka fahimci mutumin nasu fa akwai kishi. Sai suka kama kansu suma yanda bazasu takaloshi ba. Ahmad ne dai kam ya addabesa tako ina da ina, sai dai tunda ya iso AA na hannunsa ya kasa bama kowa. Har cikin rai ƙaunar yaron yake ji tamkar shiya haifa. Yace dai surukinsa ne dan shi da Maryam ɗinsa zasu haifa masa mata. Anyi dariyar zancen nashi, yayin da Smart ya ce, “ALLAH ya shiryeka kai dai. Kadai fara tara ƴaƴa sai ka fara canjawa”.
“To dama ance maka ban canja bane. Kana ganin har na fara furfura zuwan My Son duniya kuma surukina.” cewar Ahmad yana hararar Smart. Murmushi kawai yay masa da girgiza kai. Taro kam Alhmdllh, sai dai Lulu ana kammala hotuna ta koma ciki wajen Ammah da Mamy da suka basu waje suma saboda yanayin jikinta. Shima dai AA ba’a saki jiki da shi a wajen ba saboda sanyi. Sun ɗan samu gift dai-dai misali, zuwa dare taro ya tashi kowa ya kama gabansa. Gajiya ɗan kai da kawon da suka sha a yinin jiya yasa su Smart wucewa da wuri domin kwanciya.
Washe gari suka tashi Lulu nata rakin ciwon kai. Sai da Ammah tai mata addu’oi a ruwa tasha aka kama mata kan sannan. Lokacin da su Smart suka iso ya lafa mata. Tana cikin rubutu a littafinta Smart ya shigo da sallama su Ahmad biye da shi. Sai da ta saka mayafi yace su shigo. Sun gaisa da tambayar juna gajiyar taro Ahmad ya ɗan tsatstsokaneta sannan suka fito suka barsu. Smart da tun shigowarsa hankalinsa ke akan book ɗin da takema rubutu sanda ya shigo ta ɓoye. Suna fita ya kai hannu bayanta zai ɗauki littafin tai saurin buge masa hannu tana ɓata fuska. Idanun nan nasa ya kafeta da su babu walwala sam tare da shi. Duk sai taji ta daburce saboda mugun kwarijin ya mata da cika waje. Shima babu wasa a tattare da shi murya a dake ya furta, “Kinada wani abun ɓoyewa ne da kike ganin saninsa a gareni illa ne?”.
Fuska ta tsuke cikin cuna baki batare data amsa masa ba. Shima sai ya sake dakewa da koma mata Smart ɗin nan mai ɗaukar kai da manna mata hauka sanda yana drivern ta. A kausashe ya furta, “In ma baki son na sani kin makaro. Domin ɗayan littafin ai yana gareni. Banyi niyyar karantawa bane kawai dan nafi son jin komai daga bakinki ba’a rubuce ba.” Da sauri ta ɗago tana kallonsa, ya ɗauke kansa gefe kamar bai ganta ba. Sai kawai taji hawaye sun cika mata ido. Cikin rawar murya ta ce, “Da gaske kakeyi?”.
“Na miki kama da ɗan wasan kwaikwayo ne da zan miki ƙarya?. Mawaddat ɓoye-ɓoyen nan bazai kaiki ko’ina ba face cigaba da dasa miki damuwar da zata iya maidaki ga abinda kika baro. Mi kike ɓoyewa? Miye baki son a sani? A zatona ko zaki iya cigaba da binnewa kowa abinda kike kallo a sirrinki ni zan kasance ba’a cikinsu ba saboda kasancewata mafi ƙololuwar SIRINKI a yanzu. Amma bazan cigaba da takura miki son sani ba ki cigaba da riƙon abunki in dai nine bazan sake tambayarki ba”. Ya ƙare maganar kamar cikin ƴar fusata zai juya yabar ɗakin. Hannunsa ta riƙo da sauri, hakanne ya sashi tsayawa cak sai dai bai juyo ba, ya dai lumshe idanunsa da suka kaɗa sukai jajur. Itama batare data tashi ba cikin shashshekar kukan da ke sukar masa zuciya a hankali ta furta, “Aliyu ban san miyasa kake son ji ba? Babu wani abin sha’awa ko birgewa a son jin abinda ya shuɗe da ga tarihin rayuwata. Babu wani abin alfahari ko ƙayatarwa face baƙin ciki da takaici a cikin jiyana. Taya zan faɗa maka na taɓa kashe mutum da hannayen nan nawa ne?, kuma wlhy ban taɓa jin nadamar aikatawar ba har yau har gobe da ma ƙarshen numfashi na. Aliyu ban san taya kake son na faɗa maka na rasa Nanny na data raineni tamkar uwa ba a dalilin kisan da nayi ba, ta amshi laifin daba nata ba, ta rasa ranta a dalili na, Aliyu alhakinta bazai barni na rayu cikin salama ba…” ta sake sakin kuka mai tsuma zuciya.
Sosai shima yake haɗiyar zuciya, maƙogwaronsa sai faman kai kawo yake a cikin wuyansa. Idanun maza sun masifar kaɗawa. Da ƙyar ya iya controlling temper ɗinsa tare da firzar da numfashi mai nauyi ya juyo a hankali gareta. Har lokacin hannunta a cikin nasa ya zauna a kusa da ita. Jikinsa ya jawota ya rungume, hakan sai ya bata damar sake sakin kuka tana ƙanƙamesa kamar mai gudun a rabasu. Bai hanata ba, sai tambaya da ya jeho mata kai tsaye. “Taya akai kika aikata kisan kai? Dan nasan kinada dalili mai ƙarfi Mawaddat, bakiyi kalar masu aikata irin wannan laifin bisa son zuciya ba. Please faɗamin miya faru a shekarun baya a tsakaninki da Nanny ɗinki?”.
Cikin haɗiyar zuciya da shashshekar kuka ta furta, “Johanna itace Nanny na dana buɗa ido na gani a tare da ni tamkar uwa mahaifiya. Duk da dai kafin a kaini gareta na ɗan rayu a Nigeria hannun mahaifina da matarsa, sai dai babu abinda zan iya tunawa a wannan rayuwar saboda ƙarancin shekaru na. Nanny na da nake kira da Mah-mah Ta raineni ne tamkar zinariya, tana bani dukkan gata da uwa ke bama ƴaƴa duk da kasancewarta kafira. Bata taɓa cewa nabi addininta ba balle akai gata tilasta ni. Duk da na kasance mai tsiwa da rashin ji komai nai a gareta abin farin ciki ne, sai taga zan kauce da yawa ne take saurin gyara min duk da bata kasance muslma ba. Daddy na yawan zuwa gareni, dan haka nake ɗauka shi da ita duk iyayena ne, sai da na fara ɗan wayo na fara damuwa akan ƙin kwana da Daddyna keyi a gidanmu idan yazo Germany, ya yarda ya yini da ni a gida koma ya ɗaukeni mu fita yawo amma dare nayi zai wuce masaukinsa. Nakan masa ƙorafin hakan amma sai yay murmushi kawai. Itama idan na tambayeta miyasa Daddyna baya kwana tare da mu kamar sauran abokaina da iyayensu takance min aiki ne ke hanashi hakan………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣9️⃣
……..Ban fara shan jinin jikina ba sai dana ga wani yana yawan zuwa wajen Mah-mah. Atake naji na tsanesa, ko yazo gidan bana kulashi duk iya maganar da zai min, ko abu ya kawo min bana amsa. Idan kuma ya ba Mah-mah ta bani indai nasan shine ya kawo bana ci. Yana shiga damuwa da yanda nake masan har ya kasa daurewa ya sanar da Daddy. A wani zuwa da Daddy yay ne yake sanar min ai Felix yaronsa ne na amana, duk wani kai-kawo akan business ɗinsa na Germany shine ke masa. Yana zuwa wajen Mah-mah Kuma saboda harkar business ɗinne, dan itama akwai abinda take riƙe masa. Wannan zance na Daddy ya sani ɗan sakin jikina da shi, a dalilin haka na gane ashe basu da wata alaƙa da Mah-mah ɗina, A duk sanda yazo suna tattauna harkar business ɗin ne kam da gaske. Hakan sai ya sani sake sakin jiki da shi har ina kiransa Uncle, yakan ɗauke ni randa ba makaranta ya fita dani yawo yayo min shopping kamar hauka. A wani zuwa da Uncle You yayi ne yaga wannan al’amari, cikin tashin hankali naji yanama Daddy faɗan mizai sa ya bar Felix ya shiga jikina har irin hakan a matsayinsa na namiji da Business ne kawai ya haɗa su, miyasa ma ya nuna masa wannan gidan. Shi ya yarda da Mah-mah na shiyyasa damuwarsa a kasancewarta mai kula dani ilimin addini da ake neman tauyeni ne kawai. Amma sam baiji ya yarda da Felix ba sam. Naji haushin Uncle You a lokacin, dan akwai shaƙuwa tsakanina da Felix, Kun san yaro dai. Har Uncle You ya gama min hutu a wannan karon ban saki jiki da shi ba, bai damuba bai kuma daina kulani ba. Tun daga wannan lokacin naga Felix ya daina zuwa gidan. Ba irin tambayar da bamma Mah-mah ba sai tace min yayi tafiya ne mai nisa. Akwana a tashi na fara mantawa da Felix a zuciyata, sai wataran katsam gashi, a lokacin inada shekaru goma sha kusan uku, dan kaɗanne ya rage na ƙarasa tunda har secondary na shiga, duk da dai su kasan karatun nasu bawai kamar namu ne na Nigeria ba, shiyyasa ma na kammala karatuna da wuri gaba ɗaya a ƙarancin shekaru. Zuwa lokacin na manta da shi, shiyyasa ban wani sake masa ba, ga shi kuma na fara hankali. Yaso jana jikinsa amma sam naƙi sake masa, idan ma yazo gidan ko fitowa falo bana yi sam. Ni ban san ashe wannan abun naci masa rai ba har yanama Mah-mah korafi, takanyi dariya tace masa na girma ne yanzu na zama ƴammata na fara kuma mantawa da shi..
A wata ranar asabar Mah-mah ta wuce wajen ibadarsu sai ni kawai a gida da mai aikinmu. Ina ɗakina na baza books na makaranta ina dubawa, jikina daga ni sai ɗan bomshot da best, kaina ko ɗan kwali babu sai jin mutum nai kawai ya faɗo min. Raina ya ɓaci ganin Felix. Dan ko sanda inada ƙuruciya baya shigamin ɗaki ai, balle yanzu da a iyayin tashi cikin jar fata yake sakani jin na zama ƴammata ni da ƙawayena. Cikin masifa nace mizaisa ya shigo min ɗaki, ya fita bana son shirme. Maimakon ya fitan sai ya tsaya kawai yana kallona, dan gaskiya inada tsiwa sosai tun da ƙarancin shekaru na. Dariya ya shigayi irin ta shaƙiyanci, batare da ya damu da masifar da nake masan ba ya murzama ƙofa key ya nufoni. Da farko na ɗauki al’amarin nasa wasa, sai da naga yana yunƙurin rungumoni jikinsa ne raina ya ɓaci, duka na shiga kai masa ina janye jikina, ganin bazan bashi haɗin kai a yanda yake so ba ya kamani ya ɗaure, hankalina ya tabbatar min da yana son wulaƙantamin rayuwa ne. Ina kuka da roƙonsa da magiya amma bai sauraren ba ya ciremin kaya kaf shima ya cire nashi. Aliyu wlhy ban taɓa sanin minene tashin hankali ba sai a wannan ranar, tsabar tsoratar da nai da ganinsa babu sutura ban san na suma ba, sai da ya ɗiba ruwan sanyi a Despenser ɗin ɗakina ya sheƙamin na farfaɗo. Zaginsa na shigayi cikin matsanancin tashin hankali bayan dawowa a hayyacina ina tofa masa yawu a fuska, shiko ya shiga marina yana dariya, da yaga na ƙi daina zagin nasa marin ma bazai masa ba ya cire belt dinsa ya dinga dukana da ita, tamkar ya samu wata babbar mace yay min duka na hauka, har yanzu da sauran tabbunan dukan a jikina wasu basu ƙarasa ɓacewa ba. Ga jini a sayin inda ya bugeni, ga kumburin fuska data sha mari da fashewar baki, ga haɓo da dukan da yay min a gefen ido duk bai duba wannan ba ya nema haike min. Na riga na suma saboda firgita dan ya na gab da cimma burinsa na suman, shiyyasa ban san yanda akai Mah-mah ta samu nasarar shigowa ɗakin ba, ita ce ta kuɓutar dani batare da ya samu nasara a kaina ba. Kiciniyar kwanceni da dukan da yake mata ya sani farfaɗowa, sai dai kafin ta ƙarasa kwanceni ya kaita ƙasa da duka itama. Ina kuka da zaginsa a saman lips dan ko magana bana iyayi dan wahala ya kekketa mata suturar jikinta ya ɗaureta kamar yanda ya mun, a gaban idona ya keta mata mutuncinta ta hanyar mummunan fyaɗe, ya kuma juyata ta baya nan ma ya wulaƙantata. Suma ta biyu ko a lokacin dan tashin hankali. Ban taɓa sanin ana suma a dawo a suma a dawo ba sai a wannan ranar. Kaina ya dawo yana wata ƴar iskar dariya da tabbatar min sai ya wulaƙanta min rayuwa fiye da yanda yay ma Mah-mah dake kwance cikin jini face-face bata ko numfashi sosai. Ban san yanda akai wani irin ƙarfi yazo min ba na halbesa da ƙafata a gabansa, azaba ta sakashi duƙewa, pen ɗina da nake aiki da shi kafin shigowarsa na ɗauka na buga masa a wuya, banyi tunanin zai iya mutuwa ba, a haukana hakan da zan masa ai zai tashi idan aka kaisa asibiti kamar yanda naga a film yana faruwa. A take ya saki razananniyar ƙara da zubewa a ƙasa hannunsa ɗaya riƙe da gabansa ɗaya ya riƙe wuyansa. Dai-dai nan mai aikinmu ta shigo, ashe matsiyacin aikenta yay kasuwa dan ya samu damar min illa ALLAH ya kawo Mah-mah ta dawo gidan. Ihunsa ya sata shigowa, koda ta shigo taga a yanda muke mu duka ukun sai itama ta fasa ihu da komawa da gudu, itace tai kiran ƴan sanda, abinka da inda akasan kimar ɗan adam, cikin ƙanƙanin lokaci sai gasu sun iso, a gaggauce aka tattaramu duka zuwa asibiti muduka ukun. Ban dawo a yahhacina ba sai bayan kwana biyu, a hakan ma ko yaya namiji yazo kusa dani na dinga firgita kenan harda ihu ina roƙon karya cutar dani, duk wanda ya ganni sai ya tausaya min sosai. Ashe nawa wasane, dan Mah-mah ita gaba ɗaya ma brain ɗinta ta birkice, ga wata irin jijjiga da jikinta keyi, a taƙaice dai kamar ta haukace ma kawai….. Felix Kuwa ashe abinda nai masa ya mutu. Ƴan uwansa sunce bazasu yarda ba tunda kashesa akayi, wannan dalilin ne ya saka aka maida hankali akan bama Mah-mah kulawa harta ɗan dawo hayyacinta, an tattara case zuwa kotu. Daddy bai zo ba, Uncle Yousuf bai zo ba har sai da muka samu kusan sati uku a asibitin, zuwa lokacin an miƙa case kotu har an ajiye ranar zaman shari’a. Ana gobe fara shari’ar Daddy ya iso Germany, ya shiga matsanancin tashin hankali da ɓacin rai akan abinda Felix ya aikata, a ranar bai zauna ba sai da ya samo ƙwararren lawyer, washe gari aka shiga kotu. Mah-mah, bata wani bari shari’ar ta ɗauki lokaci ba ta ce itace ta kashe Felix saboda yayi mata fyaɗe ta ƙarfi. Duk yanda naso faɗar gaskiyar abinda ya faru bani da dama saboda tun a daren jiya ta roƙeni akan kar nace komai, na rufa mata asiri kar Daddy yasan ni Felix ya fara hara, dan hakan zaisa ya kalli rainon da tai min a matsayin sakaci, koma ya ɗauka dama a haka take sakaci da al’amarina tun can baya. Kawai idan anje kotu zatace a wajen cetonta ne Felix yay min wanna dukan. Yanda ta tsara ɗin haka ta faɗa a kotu, bayan gama saurarenta da lawyer da dangin Felix suka kawo alƙali ya yanke hukunci, wannan yanke hukunci ne ya sake birkita ƙwaƙwalwar Mah-mah take a wajen ta shiga wani yanayi irin na masu taɓin hankali sosai, a gaggauce aka maida ta asibiti kamar yanda alƙali ya bada umarni, hakan bai wa dangin Felix daɗi ba, dan ba haka suka so ba, sai dai babu yanda zasuyi. Sashin masu taɓin ƙwaƙwalwa aka kaita, ana kula da ita yanda ya kamata bisa tsayawar Daddy. Hankalin Daddy ya tashi matuƙa game da halin da ya ga Mah-mah ta shiga ciki, sai dai rashin sanin yanda abin ya faru yasa shi bai yi tunanin da yanzu fa akaina abin zai faru ba, tunda Felix ni yaso ketama mutunci ba, ya ɗauka kawai wajen son ceton Mah-mah ɗin nawa ne kamar yanda ta faɗa na samu wannan mahaukacin dukan, wai dan ma na samu sauƙi sosai a lokacin. Kwanan Daddy uku da zuwa Germany Mah-mah ɗina ta mutu, ta bar duniya tana kuka da sunana bakinta….”
Kuka ne yaci ƙarfin Lulu, ta sake ƙanƙame Smart da tun ɗazun idanunsa sun kaɗa sunyi jazur alamar yana kukan zuci ne. Sake ƙanƙameta yay shima jikinsa na wata irin tsuma, ji yake kamar zuciyarsa zata fashe, kukanta na sukar masa zuciya da ruhi. Tayi kuka sosai kafin ta cigaba da faɗin, “Wannan al’amari shine sanadin barowata Germany, na fahimci Daddy kamar yana tsoron maidani Nigeria ne a wannan halin saboda su Uncle You, ya maidani U.S, in da aka sake sama min sabuwar Nanny sai dai baƙar fata ce, asibiti aka sake kwantar da ni a can farko dan nima dai ina abu tamkar brain ɗin nawa ya taɓu. Na samu tsahon lokaci ina ganin likita kafin na ɗan rage firgita har Daddy ya saka ni a makaranta. Wannan shine ƙalubale na biyu, sannan sanadin abubuwa da yawa na rayuwata. Na ƙudiri niyyar yin karatu tuƙuru na zama lawyer domin kai ƙarshen irin masu halayyar Felix. Sannan kuma na kasa sakin jiki da kowa a yanzu ciki harda sabuwar Nanny ta. Banda aiki sai kuka, zaman ɗaki, a class bana shiga sabgar kowa. In har babu malami ma ina daga can gefe a takure. Duk yanda Daddy daya kasa tafiya ya barni ke lallaɓani da jana a jiki na kasa sakewa, depression yay min tasiri matuƙa. Wannan yanayin nawa ne ya jawo hankalin Alice da Luna gareni, tun bana kulasu har na ɗan fara amsa musu magana, ba komai ya jawo hakan ba sai ganin suna maida hankali a karatunsu, sannan suna nuna min suma suna cikin damuwa amma suna magance damuwarsu da wasu abubuwa shiyyasa ba’a ganewa……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣0️⃣
……..A hankali suka cigaba da shiga jikina da nuna kulawa har takai na amshi maganin da suke yawan kwaɗaitamun na sha wai zai min maganin damuwata, wannan shine sanadin komai, domin kuwa a randa na sha na farkon sai na fahimci na samu sassaucin damuwata, har takai bana iya tuna komai na wani ɗan lokaci, da ga haka aka fara, a hankali, a hankali al’amarin ya fara tasiri har aka farga damu. Malamai sun tsawata mana, saboda shekarunmu sunyi ƙaranci da shaye-shaye, sai dai babu alamar zamujisu, daga ƙarshe suka nema iyayenmu. Nanny na ce taje, amma koda muka dawo gida na tabbatar mata idan ta bari Daddy na ko Uncle You suka sani a bakin aikinta. Tasan zan iya, kuma Daddy na jin maganata, ga shi kuma ina nuna bana sonta dama. Dan haka taja bakinta tai shiru. Ni kuma sai na ɗauki matakin daina shan komai sai da dare, kafin safiya ya sakeni. Sai a week end ne nake sha da rana, wataran a gidan su Luna wataran gidan su Alice anan gidan dai bana taɓa yarda suzo ma balle musha wani ya gane, sai takai har week end ina zuwa gidajen su Alice da Luna. Sai da Daddy ya farga ne hankalinsa ya tashi, yayma Nanny na tas da tabbatar mata in fa har bata kula da aikinta ba zai sallameta. Ni kuma ya rufe ido yamun tas da faɗa dan ya fahimci na fara wasa da karatu, ya kuma haɗani da Uncle You shima yay nashi. Har lokacin babu ruwana da ko mazan ajinmu, ƙawayena biyun nan dai sune Luna da Alice. Faɗan da su Daddy sukai min ne ya dawo dani hankalina akan karatu sosai, sai kuma burin dake raina shima na ƙaramin himmar hakan matuƙa har muka kammala karatun. Mun samu damar shiga jami’a ni su Alice kamar yanda muka tsara, hakan ya sake bamu lasisin cigaba da shaye-shayen mu da yawon clubs. Sai dai inata taka tsantsan ta yanda babu wanda ke fahimtata har lokacin. Kula maza da su Luna suka fara ne ya fara sakamu fara samun matsala, sunyi-sunyi suja ra’ayina akan hakan amma ya gagara, sai ma saɓani da muka fara samu da su. Akwai wani yaro a depertment namu da ya takura min, duk da bashi kaɗai bane sauran dana karta musu rashin mutunci sukan kama kansu. Shiko naci yaƙi ya barni na samu sakat, har takai ya fara shiga jikin su Luna domin su shawo masa kaina. Amma hakan ya gagara. Ganin bazai samu nasara ba suka haɗa baki da shi aka bugar da ni, matsalar da aka samu ni ba komai ke sani buguwa irin ta galabaita ba, mukan sha abu tare da su su fita a hayyacinsu sosai amma ni ina normal sai dai ɗan yanayi, wannan yasa na fahimci manufarsu a kaina. Wannan shine sanadin daya sa na karta musu rashin mutunci irin wanda basu san zan iya ba, na kuma rabu da su dan su basu san nai mugun tsanar maza irin haka ba. Bayan rabuwa da su nasa Daddy ya canja min makaranta, naso barin shaye-shaye a lokacin sai dai hakan ya gagara dan ya shiga jikina matuƙa, sai dai ina kiyaye duk wani yanayin da wani zai iya fahimtar halin da nake a ciki, zuwa lokacin bani da Nanny, sai masu aiki, sai kuma wata yarinya da aka kawo da ga Ghana wai ɗiyar abokin Daddy ce tazo karatu. Babu ruwana da ita dan ko harakar ta bana shiga, sai mu kwashe sati biyu ban mata magana ba, koda tamun ma sai ma gadama nake amsawa. Duk ina mata wannan abunne saboda tsanar ƙawaye da nayi, bama na son ta shiga jikina da har zamuyi shaƙuwar da zata kaimu ga wani matakin kuma, sannan bana son ta san ina shaye-shaye. A haka na gama karatu da ƙyar, dan a wasu lokutan sai nayi kamar zan ɓaras saboda yanayin da nake ciki sai kuma dai na dawo hankalina da ƙyar na maida hankali. Alhamdullah na samu result mai ƙyau saboda inada kaifin basira, kuma na saka zuciyata ga abin. Na yi wasu courses da ban da ban da suka shafi karatuna har na tsawon shekara ɗaya da wasu watanni, da kaina na ce zan dawo Nigeria nayi service, dan haka kawai nake jin kewar asalina, na dawo Nigeria a tsagerata, dan bana iya ragama kowa sai Daddy Uncle Yousuf, Mommy ma rashin ɗaukar halina yasa nake shakkarta, Aunty Saliha da Aunty Naja’atu kuwa soyayyar da suka nuna min da kulawa tasani jin ƙaunarsu a lokaci guda. Dan naje Abuja ne gidan Uncle Khamil nai hidimar ƙasa ta, sai kakata Dada dake nuna min soyayya irin ta uwa, tana mun gata sosai da yimin duk abinda nake so. Case ɗin wata yarinya akan fyaɗe ne ya zama sanadin fara aikinna a Nigeria, raina ya ɓaci da abinda ya faru, har takai Aunty Naja’atu na sanar min ai wannan ba komai bane da ga cikin tarin cases na fyaɗe a Nigeria. Musamman ma a yankinmu dan gwara nan Abuja akwai wayewar kan da iyaye basa bari. Amma tacan wajen gida akan rufe zancen wai dan kada yarinya ta rasa miji ko ahalinta su tozarta sai dai iyayen baƙin ciki ya kashesu, itako ta ƙare rayuwarta a cikin ƙunci da baƙin ciki. Wannan al’amari ya tayar min da hankali sosai, sai ko na ɗauki ɗammarar zama kan ƙafafuna domin hana samuwar irin waɗan nan mata tasiri, da kuma kai duk wani shegen daya ce shi mace ce abar wulaƙantawarsa ta hanyar fyaɗe prison ya ƙare rayuwarsa acan ko ƙuruciyarsa.. Wannan shine jiyan na Aliyu. Banda baƙin ciki da takaici mi kaji a cikinsa? Babu wani abun birgewa ko ƙayatarwa”
Smart ya kasa magana, sai kukan zuci kawai, a ransa yana auna tsakanin Lulu da mahaifinta waye yafi wani zama a ƙalubale?. Sai dai duk da haka tabbas Daddy yayi sakaci da al’amarin ta, dolene a faɗi hakan, amma tunda har ya amsa laifinsa da tabbatar da kuskurensa shikenan. Lallai a yau ya koya darasin rayuwa a labarin Daddy da Mawaddat, bai taɓa tunanin ko hasashen za’a iya samun wanɗan nan al’amuran ba masu gogayya da juna. Sai dai shi fa har yanzu zuciyarsa na bashi dole akwai hannun Sulaiman akan al’amarin Lulu. Daddy bai farga bane a wannan gaɓar saboda yarda da kansa da yayi na ganin tako ina, ta kowanne motsi yana dabaibaye da al’amarin Sulaiman ɗin, ko kuma dama ya riga ya gama shirya hakan kafin shi Daddyn ya fara nashi shirin. Ya kuma haɗa da wannan itace ƙaddararta babu wata dabara ko tsaro da zai hana hakan. Duk da kuɓutar da itan da Daddy yayi hakan bai hanata fuskantar ƙaddararta da yake gudan mata a inda aka haife ta ba. UBANGIJI kenan, gagara misalin masu misali. Shi kaɗaine masanin gaibu a zahiri da baɗinin rayuwa…. Sai da ya firzar da nannauyar iskar bakinsa a kusan karo uku sannan ya ɗago Lulu da ke hawaye har yanzu a jikinsa a hankali. Sosai idanunta sun kumbura abin tausayi. Nasa juyayyun idanun ya zuba mata, tare da riƙe fuskarta a cikin tafukan hannunsa duk ya fara goge mata hawayenta da babban yatsun sa da faɗin, “Kalleni” cikin sarƙewar muryarsa da ke nuna tsantsar ɓacin rai da baƙin ciki.
A hankali ta ɗago nata Lulu idanun ta saka cikin nashi, a take gabanta yay wata irin masifar faɗuwa. Kanta ya sara. Yanayin da take jin kanta da jikinta tun a jiya ya shiga sake zafafa gudanar jinin jikinta da motsin numfashinta. Shi kam Murmushi mai sanyi ya sakar mata batare da ya fahimci halin da take ciki ba. Cikin ƙanƙanin lokaci kamaninsa suka juye mata zuwa wani abu daban kamar a mafarki. Baya taja jikinta daya fara ƴar rawa-rawa da sauri. Cikin mamaki Smart ke kallonta, kafin ya iya cewa wani abu a bazata kawai ta fasa wata iriyar gigitacciyar ƙara da ta saka su Daddy dake ƙofa na saurarensu shi da Uncle Yousuf shigowa a firgice. Hatta Abbah da Ammah da Mamy ma a ruɗe suka iso ɗakin. Riƙetan da Smart yayi sai take neman sume masa ma. Al’amarin ya bama kowa mamaki, Ummita na kuka tai kiran Usman, ya ce mata gasu nan shi da Dr Lameer ma a kusa. Ammah ce hankalinta ya kai da yanda numfashin Lulu keyi da yanda take son raba jikinta da na Smart ɗin. Da sauri ta ƙaraso garesu, hakan yasa Smart sakarma Ammah ita dan a rikice yake shima. A kuma dai-dai nan su Usman ke shigowa ɗakin. Zabura Lulu ta shiga yi a jikin Ammah da nuna Smart tana faɗin ya fita, bata son ganinsa ya fita. Yanda ta fita a hayyacinta cikin ƙanƙanin lokaci ga ciwo a jikinta yasa Abba jan hannun Smart ɗin suka fita, abin mamaki da al’ajab kamar ƙyaftawar ido sai ta koma laƙwas tana sauke numfashi. Cirko-cirko kowa yayi da mamaki, Dr Lameer ne yasa a maidata saman gado, yay ƴan dube-dubensa ya ce musu lafiya ƙalau take, dan jikinta ma Alhamdullah kaɗan ya rage. Wannan al’amari ya saka kowa mamaki, sai kallon Lulu dake sauke ajiyar zuciya sukeyi. Ganin an samu komai ya daidaita Abba da Smart suka sake shigowa. Zabura ɗaya Lulu tayi ta dire ƙasa tana neman kwasa a guje da ihun “Aliyu ka fita! Ka fita bana son ganinka, na tsaneka ka fita!”. Nanma sai da aka rirriƙeta, yayinda Smart yama kasa koda motsi. Ganin zata jima kanta ciwo akace Smart ya fitan. Yana fita abin mamaki sai ta sake komawa laƙwas. Ran Daddy ne ya ɓaci dan shi zuciyarsa bata kawo masa komai ba sai ganin da gangan Lulu keyi. Sai dai Abba ya riko hannunsa yana girgiza masa kai da faɗin, “A’a Alhaji Isma’il wannan ba abin faɗa bane abin dubawa ne. Sai dai idan shine yay mata wani abun tunda tun ɗazun suna tare a cikin ɗakin ko”.
Da sauri Daddy yace, “Babu abinda yay mata, dan duk abinda suke tattaunawa muna jiyosu ni da Yousuf. Baka san halin Mawaddat bane ba Malam Mika’il”.
Cikin damuwa Mamy ta ce, “Mawaddat wani abu yay miki ne?”.
Kai Lulu da hawaye ke silalomawa ta shiga girgizawa a hankali. Sai kuma a hankali tace, “Mamy yana koma min wani irin siffa ne mara ƙyan gani daban tsoro. Dan ALLAH kuce kada ya sake shigowa bana son ganinsa”.
Babu wanda hankalinsa bai tashi ba da wannan furuci na Lulu. Ga kuka da AA kayi duk ya sake gigitasu. Dama kuma tun jiya da dare yake kukan sai da Ammah ta dinga masa addu’oi sannan suka samu yay barci gabannin asuba. Shiyyasa ma yake ta ramuwar barcin da safen nan ko wanka ana masa yana barci. Uncle Yousuf da gaba ɗaya ya gama ruɗewa ya ce, “Ko aljanune, dan gurin nan da suke ai baya rasa aljanu ba”.
Ammah da tun ɗazun tai shiru tana nazari ta ce, “Dama Mawaddat nada aljanu ne?”………✍️
*_Lulu da Smart dole a kiraku da FURAR DANƘO kam….🥲 Sai dai in sha ALLAH maƙiya SU SHEKARA SUNA DAMU BAKU ZAME MUSU FARAU-FARAU 🤦😏🚶._*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣1️⃣
…….“A’a gaskiya, sai dai idan yanzu ta samesu”. Uncle Yousuf ya bata amsa. Iska Ammah ta ɗan furzar a hankali da cije lips sai dai ta kasa cewa komai. Duk yanda sukaso hasaso komai sun kasa, ga Smart yay masifar ɗaga hankalinsa da ƙyar su Abba suka baibayesa suna masa nasiha. Saurarensu kawai yake yi amma al’amarin na bashi matuƙar mamaki da tsoro. Wace irin masifa ce wannan suna ganin sun tsallake wancan siraɗin da ƙyar ace kuma ga wani abun daban dama yafi na baya muni. A wannan yini dai duk yanda akaso yin ɗan sauran shagalin da ya rage bai yiwu ba. Sai Daddy ne daya fita dan Ammah ta bada shawarar su wuce da Lulu Nigeria kawai. Sannan suka yanke shawarar a faɗama Baba Garko anga Lulu ɗin kamar yanda Smart ya bada shawara tun farko. Domin shi yana ganin Alh. Sulaiman ne yayo musu wani ƙullin kawai. Daddy da Uncle Yousuf da Abba ma tunaninsu kenan. Ammah ce dai keta wasi-wasi da tunani kala-kala sai dai batace wa kowa komai ba a zahiri. Ana tsaka da wannan cakwakiya kira ya samu Smart da Uncle Yousuf na gaggawa zuwa England akan harkar ƙwallonsa. Dole badan yaso ba suka wuce amma daka ganshi kasan hankalin ƴan mazan a tashe yake. Dan ma su Ammahn sun taru sun masa nasiha mai ratsa jiki da tabbatar masa matarsa na tare da shi in sha ALLAH. Nan da ƙanƙanin lokaci kuma zatazo ta samesa a inda yake. Hakan ya ɗan ƙarfafa masa gwiwa suka wuce….
Sanarma Baba Garko anga Lulu ya taimaka matuƙa. Dan cikin ƙanƙanin lokaci ya ƙarasa abinda Daddy ya fara a washe gari da daddare suka wuce Nigeria a private jet. Suma su Mommy an sanar musu, da su Aunty Bilkisu. dan haka ahalin uku suka shirya babbar tawagar tarba. An yanke shawarar wucewa da Lulu gidan Abba zata zauna a wajen Ammah. Dan haka aka rankaya can kowa bakinsa yaƙi rufuwa da farin cikin ganin Lulu da jaririn da basu san da cikinsa na sai haihuwarsa. Dan farin cikin wannan Surprise Baba Garko ranar har ƙyaututtuka yayi na musamman. Abin tashin hankali na biyu tunda aka shiga da Lulu gidan su Smart ta juyo da gudu baya sai da aka rirriƙeta. Wannan al’amari ya sake hargitsa su Daddy yayinda sauran da basu san mike faruwa ba hankalinsu ya tashi. Umma da ke a birkice tunda labarin ganin Lulu yazo musu a kunne faruwar wannan abun ya sakata faɗawa dakinta tana dariya dan daɗi ji take kamar ta ciza uwauwanta. Ana can ana haya-haya na al’amarin tana nan tana kiran Hajiya Naqiba suna kwasar dariya. Sai dai fa batun haihuwar Lulu da sai a yanzu suka sani ya taƙaita musu farin cikin nasu…
Dole aka koma da Lulu gidan Daddy ita da Babynta hankalin kowa a tashe musamman Ammah da Daddy da Abbah. Dan sun sake tabbatar da lallai akwai matsala. Aunty Bilkisu da aunty Amarya da abu yayma tsaye a rai basuyi ƙasa a gwiwa ba suka ja Ammah gefe game da zargin su akan Umma da abinda ya faru bayan tafiyarsu. Mamakin wannan al’amari ya kashe Ammah tama kasa cewa komai sai kallon su Aunty Bilkisu takeyi. Itako mitaima Umma da zafi haka a gidan nan take mata irin wannan ƙiyayyar, duk da basu tabbatar ita bace dole ko suna so ko basa so tana cikin zarginsu tunda tayi abubuwan zargin ciki harda wanda aka gani da ido. Gwaggo Sa’adah da ranta ya ɓaci ce tace zatayi magana ita kam sai dai ayi duk wacce za’ayi. Da sauri Ammah sarkin dattako ta dakatar da ita da faɗin, “A’a Sa’adah ai magana ba tamu bace yanzun. Domin yinta kamar mun fargar da itane ta sake shiri tunda zuciyarta ta riga ta mutu. Fara magance matsalar ya kamata muyi kafin mu ɗauki mataki. Yaran nan na bani tausayi matuƙa, auren kusan shekara ɗaya amma basu taɓa zaman cikakken wata ba a ƙarƙashin inuwa ɗaya gashi harda rabon haihuwa. Muyi ƙoƙarin ganin al’amarin su ya dai-daita sannan muje mataki na gaba dan ita ba komai bace face baiwa ta ALLAH shine zai mana maganinta ta inda batai zato ba.”
Badan Gwaggo Sa’adah ta so ba ta haƙura. Amma ta ɗauki alƙawarin sai ta wajiga rayuwar Ummah itama….
A wannan yanayin akai taron suna mai ƙayatarwa, dan a zahiri Lulu normal take tsakaninta da Smart da duk abinda ya shafesa ne aka nisanta su, hatta da ƴan uwansa komai normal. Dan yanda ta dinga haba-haba da su aunty Bilkisu da ma duk wanda ya ɗan uwa na Smart abin zai baka mamaki da birgeka. Bama ita ba, hatta ƴan uwanta babu wanda ya wulaƙanta mata dangin miji. Umma ce ma taso kawo gutsiri-tsoma a wajen da ƴaƴanta akan abinda bai ko taka kara ya karya ba. A take Adda Mairo ta taka mata birki da faɗin, “Sufa basa son fitina da ƙananun magana. Alkairi da farin cikine ya kawosu akan gudan jininsu. Dan haka ta kama kanta gaskiya, tunda iya ƙoƙari mutanen nan sunyi da su a wajen taron nan”. Wannan abu ya ƙonama Umma zuciya dan ba haka taso ba. Bata bari sun taho tare ba tayo gaba, babu wanda yabi takanta sai ƴaƴanta. Dan ko Mama cewa tai wlhy bazatama kanta mugunta ba sai anci komai da ita, duk da acan gida ma da suka baro wani taron za’ai.
Bayan an gama taron suna da ya girgiza sukatan su Umma da har ta fara tunanin abinda tai ɗin kamar yama warwarene ganin ɓarin kuɗin da Smart yayi, dan hatta anan gidan suma Ammah tayi taron suna sai ma kace anan maijego take, yanda aka yanka rago da sa acan gidan su Lulu anan ma ƙaton sa da ragon aka yanka, a cewar Smart basai sun damu dana can gidan su Lulu ba balle a samu masu ƙananun magana duk da yasan su Lulun bazasu ƙi kawowa ba. Alhmdllh mutanen arziƙi sun taru tako ina fiye da zato da tsammani. Yayinda komai ya tafi cikin farin ciki da bajinta dai-dai misalin da baza’a taɓa kallonsa a almabazaracci ba ko nuna fariyya….
________★
A washe garin gama taron suna Alh. Sulaiman ya iso Nigeria a hargitse. Dan a daren jiya labarin tabbatar da Lulu ta dawo Nigeria ya isa garesa. Kamar yanda mahaifinsa ya saka kuwa hakance ta faru, dan tun a filin jirgi jami’an tsaro sukai ram da shi. Wannan lamari ya girgiza zukatan Garko family sosai dama mutane da yawa da ke da alaƙa da uban da ɗan. Dan basu ɗauka Baba Garko bai haƙura ba tunda an samu Lulu. An saki Tajuddeen da ya share wata biyu a hannun jami’an tsaro yau, Baba Garko kuma yabar ƙasar sabgogin gabansa tamkar ba’ai komai ba. Ƴan ƙananun magana sun fara tashi kaɗan-kaɗan a tsakanin al’umma game da wannan cakwakiya tsakanin ɗa da ubansa. Kowa na faɗin albarkacin bakinsa, tun ƴan jarida nayi a ƙumshe har dai zancen ya fara fita a bayyane. Sai dai kowa da abinda yake faɗa akan al’amarin. Wasu suce sace ƴar ƙanwarsa yay ya ɓoye, wasu suce harda azabtar da ita yay saboda bata auri ɗansa ba. wasu suce aure yaje aka ɗaura mata akan aure da ɗan nasa. Magana dai barkatai gata nan, har abin ya fara shan kan Garko family musamman da sukaji ana neman saka waswasi akan AA wai ba’a ma san ɗan mijin Lulu na farko bane kona Tajuddeen.
Wannan magana ita ta tayarma da Daddy hankali. Ga Uncle Yousuf na tare da Smart acan England. Smart ne ya kwantar masa da hankali ta waya da tabbatar masa ai dama hakan zata faru dole, amma yayma kowa banza sai sun gama cecekuce ɗin nasu sai su san gaskiya. Abinda ke faruwar a yanzu yana cikin shirinsa akan Sulaiman ɗin. Hankalin Daddy ya ɗan kwanta ya samu nutsuwa. Amma yana mamakin wannan wane irin shirine haka da Smart da atashin farko ya ɗauki hanyar tallata abinda ke a ɓoye bayan da kansa yace yaƙin sunƙuru za’ayi. Koda yake bari ya saka masa ido yaga minene manufarsa. ai karan bana shine maganin zomon bana daman…..
Ana tsaka da wannan dambarwa aka dawo da Dada gida Nigeria. Alhamdullah ta samu sauƙi sosai kamar ba itace aka fita da ita ƙasar raga-raga ba. Sai dai ta dawo ƙasarta da tagwayen al’amura biyu masu gogayya da juna zuwa uku. Na farko shine anga Lulu, sai dai tana baƙin ciki da haihuwarta da ɗan talakan nan dai, amma dai bata yarda ta furta ba gudun karta sake ƙullama kanta tsiya ga Baba Garko da tun a sibiti ƴaƴan keta faman kiransa suna bashi haƙuri ya maidata iddarta saura kwanaki ta cika amma yay biris da su. Abu na biyu shine fitowar Tajuddeen da kama Sulaiman kuma. Wannan al’amari ya sake ɗaga mata hankali. Ta kuma sake tabbatar da Baba Garko a shirye yake da kowa kenan, dan haka ta ƙara kama kanta.
Da ƙyar ta iya bari gari ya waye tasa Uncle Muneer ya kaita gidan su Lulu. Karo na biyu kenan da zata taka Jiƙamshi House a tsohon rayuwarta. Da ga lokacin rasuwar mahaifiyar Lulu sai yau saboda tsabar ƙiyayyar da takema Daddy a baya, koda yake har yanzu ma bawai ta barsa bane, kawai tana dannewa ne saboda Lulu ta nuna mata bazata ɗauki wannan ba ana zagar mata mahaifi. Duk da kasancewar gidane ginanne a tsaye, a kuma anguwar data amsa sunanta anguwa dan kosu da ke a kusa da gidan gwamna sun san a yanzu hotoro G.R.A ɗin ta basu baya. Amma haka tsohuwar nan ta dinga wani yamutse-yamutsen fuska har abin ya bama Uncle Muneer haushi da tabbatar da Dada fa bazata taɓa ta canja ba sai dai a barta da halinta kawai dan ya riga ya shiga jininta ne. Sun sami tarba tautuntawa da ga Daddy da Mommy. Duk da dai Dada na amsa musu gaisuwa sama-sama basu damu ba. Uncle Muneer ne dai ya ware abinsa sunata shan hira da Daddy cikin mutunta juna kamar yanda suka saba. A haka su Amrah dake maƙale da AA akoda yaushe yanzu, ko makaranta sai anyi jan ido suke wucewa suka fito. Yana goye ne a bayan Afrah yana barci, yayinda Amrah ke jiran time ya cika ta kunto mashi dan dole aka koma sakama kowa lokaci har su Naseer da ake korawa makaranta da ƙyar. Dan yau Suhaib harda kukansa shi sai da AA zai tafi kamar wani ƙaramin yaro. Basu ba dake ƙanana hatta Mubeen wataran faɗa ake da shi akan ɗaukar AA. Hakan na saka Lulu farin ciki da jin ƙaunar ƴan ƙannen nata matuƙa. Su twins kansu kullum sukan kirata sama da sau uku suna tambayar ina son ɗinsu. Hotunansa kam ƙa’ida akai masa wanka sai an tura musu. Ra’is da Deen kam ai sun ma dawo nan gidan saboda AA. Mommy kanta na ƙoƙarin gyara kuskuranta akan AA ɗin, dan itace a tsaye kan kula da Lulu da yaronta duk da Iya Tabawa na iya ƙoƙarinta. Dan ana cewa za’a samo tsohuwar da zata kula da Lulu ta ce ita dai a bata dama ta maida alkairi a wannan karon. Duk da dai a tsorace take saboda sanin halin Lulu ɗin. Amma dai ganin kamar ta ɗanyi sauƙi yanzu yasata cewa a bata dama. Bako a samu wata matsalaba kasancewar a yanzu ma ga Ummita kuma, sannan da gaske al’amuran Lulun sunyi sauƙi kam, duk da idan ƴan masifar na kusa takanyi abinta………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣2️⃣
…….Sai da Mommy ta harari Afrah sannan ta sakko AA a bayanta ta miƙama Uncle Muneer da yay magana. Dada ko tai muƙuy tana satar kallon yaron. Kamar dai kunya ce ta hanata cewa a kunnto mata shi. Amsarsa Uncle Muneer yay yana murmushi da tsokanarsa irin na wasar jika da Kaka Mommy na kare masa suna dariya. Cikin murmushi ya dubi Dada da faɗin, “Dada gafa baƙon duniya kinyi sabon ɗa”.
Murmushin yaƙe Dada tayi da faɗin, “Aiko ga shi nan bai baro gida ba, ALLAH yasa iya nan ya tsaya bai ɗakko sauran halayyar ba”. Kowa ya fahimci abinda take nufi, wato kamanin AA da Smart. Amma sai duk suka basar da ita. Ganin bata da niyyar cewa a bata ɗan yasa Uncle Muneer miƙa mata shi. A dai-dai nan Lulu da su Afrah suka kaima labarin zuwan Dadan ta fito. Babu kunya ta zabura gabansu ganin Uncle Muneer na miƙama Dada AA. Cikin sauri take faɗin, “Uncle kai dai ɗauki amma dan ALLAH kada ka bata ta faki idanunku ta kashe min yaro.”
Babu wanda furucin Lulun bai dakarma zuciya ba. Cikin faɗa Mommy ta ce, “Mawaddat mike damunki? Baki gane wacece bane? Dada ce fa!”.
Babu alamar damuwa ko sassauci da ga Lulun ta ce, “Mommy sarai na gane wace. Ko a cikin dubun mutane bazata layance min ba ai ba! Dada bace?. Kiyi haƙuri Mommy ki fahimceni, tayaya zan yarda ta ɗaukar min yaro bayan tun yana ciki aka haɗa kai da ita wajen nema ganin bayansa a gaɓar da daga ni har ubansa bamu san da shi ba saboda tsabar zaluncinsu. Dan haka barni da tsohuwar nan ni na dawo a rakkiyarta. Shin mima ya kawoki gidanmu? Keda kike zaginmu kuma kin rantse ƙafarki bazata sake taka cikinsa ba saboda Daddy da Mommy sun zalunce ki?”.
A daburce Dada ta ce, “Kina da hankali kuwa Mawaddat!?”.
“Sarai nake Dada, kinfi kowa sanin haka kuma. Ko a lokacin da nake shaye-shaye na san abinda nakeyi balle yanzu da nake a cikin hankalina. Yanzu dan ALLAH bakiji kunyar zuwa wai ganin abinda na haifa ba? Abin bai miki wani banbarakwai ba hakannan? Ai nazata ko’a hanya kika ga jinina dana Aliyu kya gudu dan kunya. Baku so ba ALLAH yayi, Aliyu ɗan Aliyu Mawashi ya tabbatar muku shi ɗan halak ne. Kuma ki sanarma ɗayan Mugun ni da shi wasa yanzu zai fara…”
Rawa jikin Dada ya farayi kamar mazari. Tuni hawaye sun cika mata idanu, muryarta na rawa ta ce, “Mawaddat ni kike ma irin wannan ɗibar albarkar haka? Saboda namiji? Namijin ma da bai damu da ke ba bai taɓa sonki ba sai da akai masa tallarki da sunan auren yarjejeniya. Kin bar gidansa bai nemi inda kike ba…”
Cikin ƙyaɓe baki Lulu ta ce, “Wannan gurgun tunaninki ne Dada. Shiyyasa kika zabgan ƙarya Aliyu ya sakan ko kunya baki ji ba saboda kina son na auri shashashan jikanki da baida freedom ɗin kansa sai na ubansa. Yo ai ko maza sun ƙare a duniya gara na mutu babu aure dana auri wannan shakatafin da ko ƙirrar mazan ƙwarai babu a jikinsa soƙai-soƙai kamar wani ɗan talo-talo. Aliyu ya soni ko karya soni wannan ba matsalarki bace ba, jeki fara gyara naki matsalar auren da ya rage saura kwanaki hope ɗinki ya kufce inba haka ba wlhy azumin bana sai mun buga miki gwauruwa tashi gari ya waye….”
“Mawaddat!!”.
Daddy ya faɗa da ɗan ƙarfi cikin tsawatarwa. Cikin girmamawa ta ce, “Na’am Daddy”.
Kansa ya girgiza mata alamar ta bari. Harara ta ballama Dada ta ɗauke kanta. Mommy da Uncle Muneer abin ai ya girmi kansu. Yayinda Dada ta saki kuka tana nuna Lulu. “Ni zaki cima mutunci Mawaddat saboda na zo gidanku ganin ɗanki. Ni kike nunama kin haihu kin san zafin ɗa?”.
Baki Lulu ta murguɗa mata da taɓe baki. Uncle Muneer ya sauke ajiyar zuciya yana sake gyara zaman AA a cinyarsa da yin gyaran murya ya dubi Dada. “Dada ya isa haka dan ALLAH miye abin wani kuka anan. Mawaddat yarinya ce ai, sannan irin wannan ranar nake gudun mana dama shiyyasa nake nuna miki ki daina biyewa Yaya da al’amarinsa. Yarinyar nan itace dai zata zauna da Tajuddeen, tun farko da aka ƙulla tace muku bata so, amma kika damu kanki, kuma godema ALLAH rabon yaron nan na namiji ne, da mace ne wlhy komai zai iya faruwa ciki harda iya rasa rai….”
“Yanzu dai Manneeru kana sake goyon bayanta ta cigaba da zagina kenan?”. Dada ta faɗa cikin kuka. Da sauri ya ce, “Sam ba haka nake nufi ba Dada. Taya zan giyama Mawaddat baya ta zageki kuma. Amma kuyi haƙuri. Ina son a gyara kuskuren nan ne saboda gaba. Yanzu badan ALLAH ya taƙaita ba yarinyar nan ta kuɓuta a hannun Yaya mi kike tunanin zai faru? Ko kuma data rasa ranta a wajen yunƙurin zubar mata da ciki. Yaya yayi amfani da ke ya barki a ciki. Sannan da mijin yarinyar nan fitinanne kina ganin zai ƙyaleku ne akan yunƙurin zubar masa da ciki har sau biyu? Ga shi kunje kunce mata mijinta ya saketa! Shin aure kan aure kukai shirin mata komi ma wai shin ni na kasa gane muku?”.
Tsigil Lulu ta ce, “Abinda suka shirya mun kenan Uncle, kuma wlhy a lokacin na ƙudiri aniyar suna ɗaurashi zan kashe Tajuddeen ɗin ne sai dai nima a kashe ni!”.
Babu wanda bai kalletaba yanzu ma a razane. Itako hankalinta kwance tama miƙe tana hararar Dada da cigaba da faɗin, “Kuma ko yanzu ba haƙura nayi ba. Dan bana barin bashin gaba. Sulaiman sai yamun bayanin alaƙata da shi da ya addabi rayuwata data mahaifina, dan haka ku jira sammacin kotu dan sai munyi shari’a, idan Aliyu ya iya muku haƙuri da kawai ci ni bazan barku ba”. Daga haka tabar wajen fuuuu. Dada ta zabura zata bita Uncle Muneer ya riƙeta yana girgiza mata kai. Sai ta ƙara fashewa da kuka ta maida faɗan a kan Daddy. Wai duk shi ya kitsama Lulu taci mata mutunci tasan Lulu bata da wannan wayon. Daddy dai ko tari baiyi ba, sai Uncle Muneer ne ya shiga mata magana cikin ɓacin rai akan shi da yasan abinda zatayi kenan da bai kawota ba. Yanda yake faɗa zai tabbatar maka ransa ya ɓaci, dan sosai take cima Daddy mutunci da masa gori. Amma ko tari bai mata ba balle aje ga batun ramawa. Su Amrah ne dai suka sake zuwa suka kira Lulu. Aiko sai gata a fusace. Ranta yafi na kullum ɓaci akan abinda Dada kema mahaifinta, atake na ƴan ƙwayar ya motsa ta rufe ido taima Dada tas har sai da ta gudu dan kanta saboda ganin buyagin Lulu fa ya haifi nata. Dan yanda Lulu ke ruwan bala’i zaka rantse bata taɓa sanin Dada ba a rayuwarta balle tuna qlaƙarsu. Uncle Muneer ransa ya kai matuƙar ɓaci, da yasan abinda Dada zatazo tayi a gidan mutane wlhy dabai kawota ba. Aiko ƙin kaita yay gidan Alh. Sulaiman da tace zata duba Tajuddeen shima.
Lulu kam da bayan fitarsu Daddy ya hauta da faɗa sai ta sakar masa kuka. Dole ya fice cikin ɓacin rai dan duk da yayi shiru kalaman Dada sun matuƙar zafar masa zuciya shima, amma bazai so Lulu ta cigaba da mata tsiwa ba matsayinta na kakarya. Ya danne ne kawai saboda dattako. Lulu na komawa ɗakinta kiran Uncle Yousuf ya shigo mata. Ɗauka tai kawai ta fashe masa da sabon kuka. Ƙirjin Smart yay wata irin harbawa. Dan dama kiran nashi ne bana Uncle Yousuf ba. Haka yake yi sai ya kirata da layin Uncle Yousuf ɗin yaƙi magana. Taita faman sallama yay shiru har sai ta gaji ta katse, wani lokacin tabi kiran wani lokacin ta share. Ko tabi baya ɗauka kuma sai dai ya bama Uncle Yousuf ɗin. Dama shi burinsa jin muryartane, wani lokacin ma yakanyi sa’ar jiyo AA na kuka musamman idan darene a Nigeria kasancewar AA ɗin ya dage da musu kukan dare yanzu. Da ance ɗaya tayi babu sauran zaman lafiya kuma sai anyi sallar asuba. Wani lokacin har Daddy fitowa yake ya ɗaukesa aita masa addu’a da rirriga amma yaron nan ko’a jikinsa. Mommy tayi, Ummita tayi Iya Tabawa tayi. Lulu kam sai dai tayi tagumi kawai yana kallonsu, wani lokacin ma ba’a tashinta sai idan kukan yayi nisa ne sosai ace ta tashi ta shayar da shi. Amma yaron nan ko’a jikinsa, wani lokacin ma dan zuciyar tsiya irin ta uban baya ko kamawa.
Kasa sauraren kukan nata Smart yayi ya yanke kiran, cikin tashin hankali da damuwa ya nufi Uncle Yousuf kamar zai fasa kuka ya ke faɗin, “Kuka takeyi, ka kira kaji mike damunta Please Uncle”.
Shima Uncle Yousuf hankalinsa ya tashi, dan yasan duk abinda ya saka Lulu kuka ba ƙarami bane. Wayar ya kira tare da saka Hans-free. Kamar bazata ɗauka ba kuma sai ta ɗauka. Tambayoyi Uncle Yousuf ɗin ke mata cike da kulawa batare da ko jiran sun gaisa ba. Bata ɓoye masa komai ba ta sanar masa. Smart ya sauke nannauyar ajiyar zuciya da lumshe idanunsa da suka kaɗa sosai. Shi dai tunda ba wani abu ne ya sameta ba ai da sauƙi. Lallashinta sosai Uncle Yousuf yay, sannan ya mata faɗa da nasiha akan rashin kunyar da taima Dadan. Ya ce karta sake babu ƙyau hakan. Dada tamkar mahaifiya take a gareta. Ta bashi haƙuri da tabbatar masa bazata sake ba. Amma a ranta fa tasan ita da Dada fa ai haihata-haihata (🤣😂 ALLAH ya ƙyauta su Lulu an san daɗin ɗa🥱🚴👏).
Cikin tsokana Uncle Yousuf ke duban Smart yana faɗin, “Darun matar nan taka sai kai Aliyu, ni dama nasan wlhy bazata ƙyale Dada ba. Kuma duk a wajensu ta kwaso wannan masifar ai dan mudai a family namu babu mafaɗaci”.
Murmushi kawai Smart keyi, a ransa yana sake jinjina hali irin na Lulu. Yasan tabbas yaransa sun bani da masifa tunda shima dai ba raga masa ake ba. Wani lokacin idan tana faɗa har mamakin wai kanta baya ciwo yake yi. Tana da tsiwa sosai, ga shi sam babu tsoro a idanunta. Ita dai kawai zaman lafiyarka da ita kada ka shiga gonarta ne kawai……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣3️⃣
…….Alhmdllh sosai jego yayma Lulu ƙyau, ga Iya Tabawa na mata wani sirrintaccen gyara irin na mutanen da cikakke da ke zama a jikin mace duk da bada kanta ta haihu ba. Gefe kuma Aunty Saliha ta sake kawo wanda sukai mata gyaran aure na nasu suma yanzu. Mommy ma na nata ƙoƙarin. Sai ruwan addu’oi wajen Malam na Yakasai da ake amsowa Lulu na tsarin jikin da yanayin da take ciki game da Smart. Wannan ƙoƙarin Ammah ne da Abbah. Dan ita kanta Ammah kan zauna da kanta tai mata addu’oi a cikin ruwa da ma ruwan zam-zam shima AA ana bashi.
Sai Daddy da ya kawo mata malama har gida tana ɗora mata karatun addini saboda Ummita zataje ganin gida itama. Da yake Lulu tasa abun a ranta hatta Mubeen zaunarwa take ko su Amrah su ƙara mata karatun. Gefe guda kuma tana ta ciku-cikun yima ƙungiyarta rigester shima da taimakon Daddy da Uncle Khamil na Abuja da shima ya bata goyon baya. Koda wasa bata son tuna Smart, dan ko AA ta kalla babansa yazo mata a rai kanta ya dinga wani irin masifar ciwo kenan dake tayarma kowa na gidan hankali. Inda aka yankata Alhmdllh yana sake warkewa, Aunty Khadijah matar Coach ce ke zuwa dubata kullum babu fashi, idan abinda ya kama taje asibiti ne kuma sai ta shirya Mubeen ya kaita suje suga likitan su dawo. Da Ummita zata wuce shatara ta arziƙi Daddy ya haɗa mata, itama Lulun ba’a barta a baya ba, Uncle Khamil ne da yazo ya wuce da ita duk da dai jirgi sukabi zuwa Abuja tare, dan Lulu ta gargaɗeta zuwa ɓagwai saboda gudun mutanen Alh. Sulaiman kar su cutar da ita ko iyayyenta.
★A ɓangaren Ammah tsaye take wajen kaima UBANGIJI kukanta akan dai-daituwar zaman waɗan nan ma’auta. Tare da yawaita sadaka da azumi. Yaranta kaf basu zauna ba har ƴan uwanta kasancewar suna da haɗin kai. Yayinda itama Ummah ta kasa zaune ya kasa tsaye wajen sake lafto sabbin asirai kala da iri akan Ammah da Smart kai harma su Aunty Amaryar ba bari tayi ba. Dan a kwanakin nan da ƙyar suka samo kan Abba da aka nema juyarma da kai. Sai Alhmdllh al’amarin baiyi nisa ba ya sake shi, hakan ya tada hankalin Ummah kam sosai, dan ba ƙananun kuɗi ta kashe a aikin da akaima Abban ba, amma sai gashi ya tafi a banza cikin ƴan kwanaki ƙalilan….
*_UK LONDON_*
Hassada ga mai rabo taki ce, sannan duk abinda UBANGIJI ya ƙaddara shi a matsayin naka babu wani mahaluki a duniya da ya isa canja wannan ƙaddarar. Dan kuwa a lokacin da Ummah ke can tana faɗi tashi akan abinda bata iya jayayya da shi ba anan ƙasar England ƙaramin labari ne ke neman canja kansa akan Aliyu Mika’il Idris Mawashi, wato Smart Mawashi zuwa babban gaske gagarumi. Dan fa manyan clubs da ke zawarcinsa ta ƙarƙashin ƙasa sun fara bayyana kansu a fili yanzu. Wannan yasa aketa faman kai kawo da dambarwa tun barowarsu Canada shi da Manager ɗinsa Uncle Yousuf. Sosai ake ta kai ruwa rana da bata kashi a tsakanin Coach’s ɗin mayan clubs ɗin. Shi dai Smart ya duƙufa gayama UBANGIJI da neman zaɓinsa. Dan bashi da wani zaɓi sai nashi. Yayi alƙawarin duk inda ya tsinta kansa zaiyi aiki tuƙuru in sha ALLAHU duk da a cikin zuciyarsa yana da club ɗin da yafi so da ƙauna kuma gashi a cikin masu zawarcin nasa. Amma sai bai Zafafa ba ya bar ma UBANGIJI komai sai su Uncle Yousuf da keta kaiwa da komowa shi da Coach ɗinsu na Queen City da duk manyan masu faɗa ajin club ɗin.
Sosai mahawara ta ɗauki zafi a tsakanin manyan clubs guda uku da suka riƙe wuta fiye da sauran, dan kowa ya gagara janyema kowa. Sannan duk sun zuba manyan kuɗaɗe akan Smart ɗin masu girgiza zuciya. Abu kamar wasa ƙaramar magana ta sake zama babba. Dan manyan gidan jaridu na duniya musamman a fanin ƙwallon ƙafa sunyi ƙur da idanunsu akan wannan batu domin ganin wazai ɗauki wannan lu’u-lu’un a cikin juji. An buga an turza an kai matuƙar kai ruwa rana kowa yaƙi sakarma ɗan uwansa, dole aka tafi mataki na biyu wato jin ra’ayin Smart game da wane team yafi sha’awa shi a ransa. Tun farko Smart nada ra’ayinsa dama, amma ya zaɓi barma UBANGIJI zaɓinsa. Har a yau da aka kai wannan matakin na jin ra’ayinsa bai ji zuciyarsa ta canja da ga abinda ta ke so ba tun yana da ƙuruciya. Dan haka bai wani basu wahala ba ya faɗa musu zaɓinsa wato *_ARSENAL FC_*. hankalin sauran clubs biyun da sukai gogayya da Arsenal ɗin ya ɗaga, a take suka ƙara kuɗi akan wanda suka saka a farko, amma dai Smart nakan bakansa Arsenal ɗin dai, dole suka haƙura dan aikin gama ya gama Arsenal tayi nasarar siyensa da kuɗi kimanin dala Miliyan arba’in.
Duk wani masoyin Smart a wannan rana yana a cikin matuƙar farin ciki mara misali, Ammah duk dauriyarta sai da tai hawaye lokacin da Uncle Yousuf yay kiransu yake sanar musu al’amari fa ya kai girman da aka daɗe ana fata. Sai kuma addu’ar cigaba da samun nasarori ga Smart ɗin. Amma wannan tsanin kam an haye sama ƙololuwa.
Sun ɗanyi zaman meeting meeting da ƴan cike-cike na tsarabe-tsaraben da aka san ƙwallo da shi su da Manager ɗin sa Uncle Yousuf da shi kansa Smart ɗin. Kafin dai a ƙarƙare ya saka hannu a ƙarshe. Da ga haka akaje matakin duba lafiyarsa ciki da bai. Alhamdullah nan ma normal an samesa da cikakkiyar lafiyar jiki dama ta sassan jiki. Bayan kammala waɗan nan ya ziyarci Arsenal camp domin yin hotuna da gabatar da shi ga teammate ɗinsa. Ya samu tarba fiye da yanda yay zato da tsammani ga teammate ɗinsa. Dan tunda suka shiga cikin camp ɗin bakinsa bai bar ambaton ALLAH ba. Kwarjininsa da hasken musulunci ya sake ƙawatashi a garesu da girmama mutuncinsa. Sunyi hotuna da duk abinda ya dace a wannan ranar kafin a wuce mataki na gaba. Wato gabatar da Smart Mawashi ga fans.
Duk wani masoyin Arsenal ya halarci babban stadium ɗinsu da ke a cikin birnin London. Wasuma da ga ƙasashen ƙetare suka zo domin ganin sabon yaron na Arsenal da za’a gabatar saboda soyayyar da sukema club ɗin. An cika matuƙa da har sai da Smart ya dinga jin kansa na sara masa. Ga kuma masu kallo a television. Amma ya daure bakinsa na cikin ambaton ALLAH ya fuskanci masoya. Wani irin ihu da stadium ɗin ya ɗauka lokacin da yake shigowa fuskarsa ɗauke da sassanyan murmushi yana mai ɗaga musu hannayensa biyu yay dai-dai da wanda su Mubeen suka ɗauka suma a cikin falon gidansu da Lulu ce kawai babu tana can ɗakinta tana barci. Hatta AA na a hannun Daddy dan har shi ake wannan kallo. Fitowa tai a ruɗe, sai dai ganninsu duk suna kallon ƙwallo a tv kuma duka gidan ya sata tsayawa turus cikin dafe kai da jan tsaki. Babu ma wanda yasan tanayi dan hankalinsu bama ya wajen. Cikin jin haushi ta juya ta koma duk da tayi mamakin ganin harda Daddy da su Iya Tabawa wai ake kallon ƙwallo yau a gidan. Abu ne ita dai da bata taɓa gani ba. Ta dai san Mubeen nayi da su Hussain idan sun zo. Amma kosu Amrah ta sha jin suna faɗa da Mubeen idan zai kalla ƙwallo ya hanasu su kalla film. Amma wai yau sai gashi ƙwai da kwarkwatar gidan ta gani. Abinda ma Lulu bata lura da shi ba shine harda masu wanki duk suna a falon, dan suna da ga ƙasa ne zaune yasa bata gansu da ƙyau ba… Kamar yanda a gidan Daddy suke kallo a gidan su Smart ɗin ma hakane. Dan su Mubarak ne suka cika gidan da abokansu da samarin anguwa. Yayinda ba’a bar Abba a baya ba da ga shi har Ammah da sauran yaran gidan sun cika a falonsa danƙam dan shi yasa a tattaro kowa yazo. Ran Umma da Mama a mutuƙar ɓace yake. Zuciyar Umma bata nema fitowa ta baki ba sai da aka nuna Smart na shigowa cikin tsakkiyar tarin tawagar turawan nan yana ɗan wasa da ƙwallo, stadium ɗin ya ɗauki ihu kamar zai tsage. Sai kuma sanda aka ɗaga rigarsa mai lamba tara yanda suka ɗauki ihu mai jijjiga kunne ita zuciyarta suke jijjigawa, dan a bazata kawai sai ta fashe da kuka. Da farko babu ma wanda ya lura da ita sai da Huwaila ta ce, “Ummah ke kuwa miya sakaki kuka? Ko duk farin cikin ganin Yaya Hydar ɗinne?”.
Lokacinne hankalin kowa ya koma kan Umma. Sai dai kafin ma wani ya iya cewa wani abu ta miƙe cikin rangaji kamar wadda tasha tai marisa ta nufi ƙofar fita. Ƙayataccen murmushi Abba da Ammah suka saki kusan lokaci guda. Yaranta dama duk wanda ke wajen zasu ɗaga hankalinsu su bita Abbah ya ce kowa ya koma ya zauna, idan kuma wani ya bita sai ransa ya ɓaci. Dole sukabi umarninsa. Da ga baya ma abinda ke faruwa ya ɗauke hankalinsu kowa ya manta da batun wata Umma can….
Sosai Smart ke jin farin ciki a ransa mara misali dan harda hawayen farin ciki ganin yanda waɗan nan ɗunbin al’umma suka amshesa da taruwa domin shi. Bakajin komai sai ambaton sunansa a wajen, _Smart Mawashi, Smart Mawashi_ dai. Yanda ma suke ambaton Mawashi ɗin abin dariya. Abinda ya ƙara tabbatarwa da mutane Smart Mawashi ya amsu yanda a yinin ranar kawai an saida copy na rigar JC mai ɗauke da sunansa kawai ta kai kimanin dubu hamsin. Wannan al’amari ya matuƙar ɗaukar hankalin mutane da gidajen jaridu. Yayinda masu fashin baƙi akan harkar ƙwallon ƙafan keta nasu aiki. Gida Nigeria musamman arewaci kuma garin Kano sun shiga matuƙar alfahari da ganin ɗan su yau a wani mataki na rayuwa da sai ɗan baiwa mai Sa’a kawai ne ke takawa. Hatta da social media babu abinda ke kai kawo sai hotunan Smart Mawashi da tarihin rayuwarsa. Hatta da hotunan bikinsa ranar sai da suka dawo sabbi a yawon media. Sai a lokacin ne Lulu tasan wainar da ake toyawa. Ita kasa ma fassara al’amarin tayi sam. Cikin sauri ta shiga bincike-bincike a media. Sai ko gashi ta ga duk abinda take buƙatar. Tsabar yanda al’amarin ya dakar mata zuciya bata iya furta komai ba. Dan datace ma zata tsananta tunani ko maganar Smart ɗin matsanancin ciwon kai da tsanarsa da take ji ke dawo mata sabuwa. Dan ma Alhmdllh zuwa yanzu akwai ɗan sassauci a a al’amarin kasancewar addu’a da aka duƙufa yi babu dare babu rana. Yau ɗin ma dai ta yini da ciwon kan, dan har dare tana kwance tana fama har sai da Daddy ya shigo yay mata addu’oi….
Bayan Smart ya fito da ga stadium hirarsa da ƴan jarida ta zama abu na biyu da ya sake zama babban topic a kansa a wannan yini. Ya bada tarihin rayuwarsa da yay matuƙar taɓa zukatan mutane harda masu hawaye, dan ma ya ɓoye kaso tara cikin goma ya bayyana abinda yake da buƙatar duniya ta sani ne kawai. Ya bayyana irin yanda ya tashi da son ƙwallo a zuciyarsa da taimakon da Abdull-Hameed Coach yay masa a rayuwa da matsalolin da ya samu da ga baya. An masa tambaya akan dalilinsa na zaɓar team ɗin Arsenal duk da sauran clubs biyu da suka riƙe wuta a zawarcinsa sun sake ƙara kuɗi amma yace Arsenal ɗin dai. Sai yay murmushi da faɗin “Arsenal club ne da tun yana yaro yake matuƙar so, sannan club ne mai ɗunbin tarihi da kuma ya ajiye tarihi da tarin masoya a duniya, sannan club ne one of the best in the world. Sannan yana da ƴan wasan da yake matuƙar so da kallo a matsayin madubinsa a cikin club ɗin irinsu Terry Herry. Patrick Vieira da sauransu…….”✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣4️⃣
……..A ɓangaren Ummah tana shiga ɗakinta ta sake tsagewa da kuka, a haka ta hau neman layin Hajiya Naqiba.
“Na shiga Uku Aminiya Abban Salim ne ya mutu?”. Cewar Hajiya Naqiba a rikice jin Umma na ɓarza kuka.
“Ba garama mutuwar ba zan haƙura dole Aminiya. Ashe malamin nan yaudarata yake shima duk irin maƙudan kuɗin dana zube masa. Gonata ta gado fa na ɗaga na sayar na bashi kuɗin aikin nan amma ace wai duk a banza nayi, yau sai ga shegen yaron nan mai taurin ran tsiya a tsakkiya Turawa kamar zasu cinyesa dan soyayya. Wai wani ƙungiya na kwallo asinal yake ko uwarmi ne ma oho musu suka sayeshi da wani uban kuɗi da har yanzu ma zuciyata da ƙwaƙwalwa ta sun kasa haɗawa dai-dai, wai zai musu ƙwallo na shekara biyar. Shike nan na mutu Aminiya, duk wahalar da nake akan yaron nan dai abanza take cigaba da tafiya”.
“Tofa babbar magana, wai shi Hydar ɗin ne yakai wannan matakin na shiga ƙungiyar Arsenal? Shin ko shine ma ɗazun Maheer ke ban labari cikin zumuɗi wai wani matashi Smart ɗan Kano ya zama babban gwaska a duniya, yanzu hakama yana nan gidan Alhaji Sammani wai suna kallo ko ana nunashi”.
“Matsiyaci haihuwar asara shine. ALLAH ya tsinewa uwarsa ma bashi ba. Na tsani matar nan fiye da yanda na tsani mutuwata, duk irin wahala da kai-kawon da nake a kanta da faɗi tashi kullum abbanza suke tafiya. Narasa wace irin baƙar tambaya ke ga Hafsatu”
“Humm Aminiya kar kice haka, kin manta nasarar da kikaci ta tsahon shekaru yaron nan ko filin ball bai iya shiga, ga tsanar da Abban Salim yay masa. Sannan a yanzu haka fa akwai asirin dake jikinsa wanda ya gagara zama da matarsa waje ɗaya….”
“Na fara ji a raina asirin nan bai kama shegen yaron nan ba, matar tasa kawai ya kama dai kamar, kuma mayen yaƙi sakinta. Malam yana ɓoye mana ne kawai”.
“Tunda dai har ya kama matar tasa ai ya wadatar damu. Ki kwantar da hankalinki dan ALLAH yanzu ma bamu makara ba. Wajen Na-zuru zamu koma tunda dama shine yay masa wancan ƙullin goron na farko, irinsa zai sake mana ko ya shiga filin ya yanke jiki ya faɗi basai muga ta ƙafafa ba. Sannan kisa ranki a inuwa, wannan maƙudan kuɗi da kikaji ba nashi bane ba, haka naji Maheer nacewa da nake masa faɗan shi miyyasa bazai zo ya koya ƙwallon ba.”
“Kai dan ALLAH wai da gaske kike? To kudin na waye?”.
“Ni ban sani musu ba, kamar dai yace wai ko kungiyar daya bari ne ai da kuɗin, shi za’a yanka masa nasa albashinne.”
“Kai amma har na ɗan jin sanyi, shegiyar uwarsa sai muga ta hura hanci, ashema kuɗin na wasu ne shasha ɗan ya koma bawan turawa bata farga ba”.
Dariya suka kwashe da shi kamar suna kusa da juma….
Niko na ce, “Hummm!”.
★Sosai abinda Umma tayi ya tsayama Abba a rai, har ya shiga dogon nazari akanta. Sai dai baicema kowa komai akan hakan ba. Itama baice matan ba. Ya dai ɗauki ɗammarar saka ido a lamarinta domin tabbatar da abinda ransa ke raya masa…
★Ammah kam ko’a jikinta, dan ita zuwa yanzu lamarin Ummah bai wani damunta sosai. Face dagewar da tai da addu’a ita da zuri’arta domin kariya da ga sharrinta. Dan duk yanda Gwaggo Sa’adah taso ɗaukar mataki ta hanata, acewarta su jira sakamako na zuwa akan kowa…..
*_6 MONTH’S LATER_*
Abubuwa da yawa sun faru masu tafiya da nasarori da kalubale a cikin waɗan nan watanni da suka kasance kusan tara da haihuwar Lulu. Ƙalubalenta na farko mai kuma girman gaske shine shiga tsakaninta da mijinta uban ɗanta da akai ta hanyar sammu mai ƙarfi. Nasararta ta farko komawa islamiyya neman ilimin addini tuƙuru tare da maida hankali matuƙa duk da ta koma bakin aikinta. Sai wannan gaɓar ta kuma samu nasarar kafa ƙungiyar da take buri data samu tallafin ƙarfafa gwiwa da ga iyayenta da kakanta har ma da ƴan uwan haihuwar makaifiyarta. Nasara ta uku kafa business ɗinta data jima tana buri na turare, tana kawosu daga ƙasashe daban-daban, ana kiran ƙaton shagonta da suna *_LULU’s ƘAMSHI_*. Nasara ta huɗu ƙyaƙyƙyawan yaronta da kamaninsa ke ƙara fitowa dana mahaifinsa nata ƙara wayo gashi cikin ƙoshin lafiya da kuzarinsa. Alhamdullah kuma yana a cikin kariyar UBANGIJI shikam. Dan duk da irin hare-haren da su Umma suke kawo masa ALLAH ya kiyaye abinsa yaron nan ko gezau. A yanzu haka ya fara miƙewa ya ɗan dafa kujera alamar dai yana son taka ƙafa. Ana kaisa wajen Ammah ya yini abinsa, kasancewar yana shan koko kuma gashi baida damuwa akwai haƙuri yasa sai ya yini lafiya sannan a maidosa. Itama su Asma’u kanzo su yinin mata anan. Su aunty Bilkisu kansu kan zo suga AA da gasiheta lokaci-lokaci. Itama kuma tana zuwa gidajensu har ta yini. Can gidan ne dai bata iya zuwa. Dan kota gwada hakan baya yiwuwa. Wannan abu na cimata rai dan tana so da ƙaunar Ammah a ranta. Wannan soyayyar da ga ALLAH ce. Shiyyasa itama Ammahn kan leƙosu lokaci-lokaci musamman idan ance AA na mura haka ta haƙora. Sosai shaƙuwa ta shiga tsakaninta da dangin Smart. Dan hatta samarin su Mubarak sukan zo gareta a ɓoye batare da sanin iyayensu mata ba. Duk watan duniya kuɗi kan shigo account ɗinta da ga Aliyu, sannan akan kirata da number ƙasar England. Sai dai kota ɗaga ba’a magana, sai ita zata dinga hello-hello da ga ƙarshe a yanke kiran. Takan ji haushi tace bazata sake ɗagawa ba. Amma da an kira bata iya haƙuri sai ta ɗaga ɗin…
★A gidan su Smart kam nasarori da ƙalibalen suma dai basu tsallake su ba. Sai dai Alhmdllh a ɓangaren Ammah babu abinda zata cema UBANGIJI sai godiya. An tsaida Ranar auren Maryam da Ahmad. Yayinda ɗaukakar da ALLAH ya bama Smart ta sake fiddota a cikin ƴan uwa dama jama’ar gidan har da dangin Abbah. Smart ya dakatar da Abbah fita kasuwa duk watan duniya ya yanka masa albashi shi da Ammah a cikin albashinsa da ake biyasan duk sati-sati. Sannan Ahmad zai kawo kayan abinci bisa Umarnin sa.
Wannan abu na ƙara ɗaga hankalin Umma har ma da Mama. Sai dai banbancinsu ita mama kan balbale nata yaran da faɗa ne akan suma su san ciwon kansu su dinga ma mahaifinsu in ba hakaba smart zai ƙwace dukkan power ɗin su, sannan ita bata bin malamai, kishi ne dai irin na matan bahaushe da jin ƙyashin cigaban kishiya. Itakam Umma tsantsar hassada da baƙin ciki sunbi sun kanainaye mata zuciya da ruhi. Ta kasa zaune ta kasa tsaye. Duk ɗan abinda ta samu suna a yawon malamai da bokaye ita da Hajiya Naqiba aminiyarta. Aikin suke iya ƙarfinsu amma basu sake jin wani sabon abu ba bayan zaman Lulu gida. Ga malamin nata ya tabbatar mata akwai fa matsala idan aikin bai kama Smart ba shi. Dan su duka biyun akai musu ai akan su tsani juna. Wannan dalilin yasa take ta faman bibiyar al’amarin Smart dan taji shi ya wajensa yaya akan matar tasa amma ta kasa samun kowacce irin mafita. Ga lamarin Huwaila na caja mata kai. Dan ta girmi Maryam amma har yanzu babu tsayayye, saka auren Maryam kansa ya hargitsa mata lissafinta. Balle da taji cewar itama mai hannu da maiƙo zata aura. Wayyo ina wuta ta saka Ammah ne. Ta rasa wane irin sirri keda Ammah ɗin da dukkan ƴaƴanta suke auren ƴaƴan masu kuɗi. Yanzu dai abu biyu ta saka a gaba. Wato tarwatsa rayuwar Smart da rusa auren Maryam. Duk ta fige ta lalace a tsaye saboda saka wa kai musiba. Itace kullum faɗa da ƴaƴa akan su bata kuɗi, musamman ma Salim dake nuna mata shi fa ya gaji da wahalarta, mitake da kuɗi wai kamar wata ƴar caca..
Duk abinda take a yanzu idon Ammah ƙyam yake a kanta, dan haka ta dake dagewa da addu’oi da sadaka.. Tare da kiyaye duk wani abinda Umma zata basu koda abincin gidanne yanzu ranar girkin Umma sai suka daina ci, miya Ammah ke musu mai yawa tasa a freight, duk ranar da Umma tai girki sai tayi musu abinci a a ɗaki suci, na Ummar a fitar waje aba mutane cikin hikima.. A tunanin Ammah Abbah bai san mike faruwa bane, sai dai idonsa na akan komai yana dai biye yaga iya gudun ruwan kowannensu musamman ma Ummah..
________★
A garko family kam abubuwane keta ƙara tsamari. Abu na farko shine Baba Garko dai tunda ya tsallake bayan kama Sulaiman bai sake dawowa ba, sai labarin a washe garin da Dada taje gidan su Lulu suke jin cewar an ɗaura masa aure matar ma ta bisa. Ranar sunga abinda ya girmesu a wajen Dada. Dan zaman ƴan bori tayi a gaban surukai ta saki ƙaƙƙarfan ihun da ya nema girgiza ginin gidan. Ba ita ba su kansu yaran hankalinsu ya tashi, a ganinsu mi mahaifin nasu zaiyi da wani aure a shekarunsa haka, kuma abin mamaki wai ma budurwa ya aura sa’ar ƴaƴan cikinsu. Matansu kam dai wannan al’amari yay musu daɗi, sai dai suna ƙoƙarin dannewa a gaban mazan nasu.. sai an koma gefe asha gulma da dariyar Dada..
Sai da Baba Garko ya kwashe watanni kusan shida da amaryarsa suna yawan hutawa a ƙasashe sannan suka dawo Nigeria da cikinta da ya fito kowa na gani. Ƙyaƙyƙyawar mace ƴar gaye mai tarin ilimin addini dana boko. Sannan gata yarinya ƙarama, dan bazata wuce sa’ar Lulu ba ma. Da gani dai kasan kuɗi ta gani ta shige, duk da dai Baba Garko ba baya ba wajen ƙyau amma tsufa ai ya ƙwace komai sai godiyar ALLAH kawai. Wannan ciki ya saka ƴaƴansa jin matuƙar kunya, sai dai babu damar yin magana ya maka wankin babban bargo, dan shi ko’a jikinsa. Kuma yace dole su girmama masa mata. Suna son sake bashi haƙuri akan mahaifiyarsu suna jin tsoro, dole sukai gum da bakunansu.
Washe gari Daddy da Uncle Yousuf sukaje gaishesa suma da masa murnar aure anan ne su dai suka fidda kunya da tsoron suka roƙesa akan yay haƙuri itama Dada ta dawo. Ai an mata gargaɗi. Shima Alh. Sulaiman ai masa afuwa dan ALLAH ya dawo cikin iyalinsa. Bai tanka musu ba dai, sai sakawa da yay Uncle Yousuf ya kira masa Smart a waya. Yako kira masa shi suka gaisa. Yana jin ƙaunar yaron matuƙa yanda yake bashi girma. Yay masa faɗa akan rashin kiransa su gaisa, tare da tayasa murnar cigaban rayuwa da ya samu. Yace shi ai bai sani ba sai kwanan da ya gansa ana hira da shi ya shiga mamakin kamannin har yay kiran Daddy shine fa yake tabbatar masa da shi ɗinne. Haƙuri Smart ya bashi cikin girmamawa da tabbatar masa zai gyara insha ALLAH. Cikin gamsuwa Baba Garko ya sake saka masa albarka. Sai kuma ya tambayesa yaushe ne zai zo ya ɗauki iyalinsa. Ɗan jimm Smart yay na wani ɗan lokaci, kafin ya firzar da numfashi yana jan ajiyar zuciya. Cikin tausasa harshe ya ce, “Baba yanzu ni lokacin nawa ne sai a hankali, dan gashi ana tsaka da fara buga wasan premier link ne. Sannan kuma itama bana son a takura mata har sai idan itace da kanta ta yarda zata nemeni nake ganin hakan zai fi zama masalaha, itama bazataga an takura mata ba kamar farko”. Murmushi irin na manya Baba yayi. Tare da cewa, “Shike nan shawaranka yayi sosai”. Daga haka suka ajiye wannan maganar Smart ya koma bashi hakuri shima akan maida Dada da sakin Alh. Sulaiman. Acewarsa shi ya yafe komai ya wuce a tari gaba……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣5️⃣
……..Wannan roƙo nasu Smart da Daddy da Uncle Yousuf harma da Abba da shima yazo masa murnar ƙara aure akasha hira da barkwanci na tsoffin abokai bayan sati biyu Dada ta dawo. Dawowar data zame mata matsanancin jin zafi. Gashi ba abun tace bazata dawo ɗin ba ta rasa sauran damarta. Ga muzantatan da surukanta keyi na sake ɗaga mata hankali. Ta samu gida fa komai ya sauya. Hatta masu aiki kowa dai Aunty Amarya dai aunty amarya dai. Dan yarinya ta kwantar da kai tana cin garar arziƙi abinta. Ta kuma kame kowa na gidan da ƙyautatawa bayan uban gayyar Baba Garko da taima ram da zuciya yake jinsa kamar wani ɗan shekara talatin, dan more tsufansa yake hankali kwance ya manta da batun wata aba Dada… Ganin cikin amarya da Dada kejin wai-wai a bakin mutane ya sake ɗaga mata hankali ta ɓarke da kuka. Wai itace yau tsofai-tsofai da kishiya, kishiyar ma sa’ar jikokinta kai jama’a wane irin cin zarafine wannan Alhaji Sufi yay mata ne ita kam a duniya, duk wahalar da tai a ƙuruciya na hana wata shigowa gidanta sai a wannan gaɓar za’ace wai ga ɗan uba a cikin zuri’arta. Ga shi Baba Garko yaƙi ko saurarenta tunda ta dawo, duk ranar girkinta fa zai yi kamar suna tare amaryarsa bata zuwa inda yake, amma kuma bai barin itama Dadar tazo. Ko kuma ma ya ƙirƙiri tafiya. Bayan wata ɗaya da dawowar Dada yasa aka saki Alh. Sulaiman shima…..
______★
A ɓangaren uban gayya kam al’amura sai dai Alhmdllh. Dan komai yana tafiya fiye da yanda akai fatansa. Ya zama cikakken ɗan wasan Arsenal da yanzu duniya ke kallo ta faɗa da kiransa *_GWARZON ZAKI_* Sunan Smart Mawashi sake dilmiya yake a duniyar ƙwallon ƙafa. Dan a yanzu haka ya fara taka sabuwar rawa a sabon team ɗin nashi na Arsenal. Duk da kuwa wasanni uku kenan suka buga kacal. Sai dai aduka wasan babu wanda bai saka musu ƙwallo ba. Wannan ya sake jawo hankalin al’umma kansa tako ina a duniya. Ya zama ɗaya daga cikin matasan yara masu tashe a duniyar ƙwallon da ake faɗa ake ma kan faɗa a kowane yini. Al’amarin matarsa bawai baya damunsa bane, ya miƙama UBANGIJI al’amarinsa ne kawai da fatan cinye waɗan nan jarabawoyi kashi-kashi. Shi kaɗai yasan abubuwan da yake jurewa a irin wannan tsukun. Amma yana matuƙar begen matarsa a kusa da shi har ma da gudan jininsa takwaransa…..
____________★
Yau ma a gajiye ta dawo gidan kamar kullum Ummita biye da ita da tarkacenta. Tunda aka kammala bikin buɗe ƙungiyar nan tata bata huta ba. Ga aikin kungiya gana office ga karatun islamiyya ga shago. Dan rainon AA dai bazatace komai ba kusan Mommy da su Afrah ne keyi da Iya Tabawa. Tsakaninta da shi kawai ta shayar da shi. Kasancewar ma yana shan tea da koko hankali kwance bai cika damuwa ba. Shiyyasa ma bata fita da shi ko’ina. Ba kuma ya kuka dan shi ɗin mai iyayene da yawa. Itada kanta ma wani lokacin har tausayi yake bata da rashin samunta yanda ya kamata. Amma yaya zatayi.
Tunda sukai sallama AA da ke a bayan Suhaib na masa doki ya fara zillo. Saukesa yay suna masa dariya. Ya rarrafo da saurinsa zuwa gareta. Kamar yanda suke dariyar itama dariyar takeyi. Daukarsa tai ta jefa sama ta cafe tare da rungumesa tai masa kiss. Shima yay mata a kumatunta biyu. Lakace masa hanci tayi cike da farin ciki da jinjina wayonsa. A kullum kamar ana ƙara masa wayo ne. Baya magana dai sannan tafiya bata nuna ba, amma idan ka gansa bazakace watansa tara ba. AA akwai zafin nama da ɗankaren wayon tsiya. Shiyyasa ɓarna babu kama hannun yaro. Idan aka kaisa hira wajen Daddy har korosa yake saboda ɓuruntu. Hakama Mommy sunta faɗa kenan.
Cikin zubewa a kujera Lulu ke faɗin, “Wayyo ALLAH ku bani ruwa kafin na shiɗe Please”. Amrah na dariya ta miƙo mata ruwa da kofi, kofin ta ture ta ɓalle murfi goran ta kafa kai kawai. Neman ƙwacewa AA yake tana buge masa hannu, bata kulashi ba sai da ta kusan shanyewa ta bar masa ɗan kaɗan sannan ta bashi.
“Wai lallai aunty Lu.. kinji ƙishi fa”.
Cewar Mubeen dake ƙoƙarin ɗaukar AA da ke miƙa masa hannu. Dan shigowarsa kenan shima da ga makaranta. Tace, “Ka bari kawai broth wlhy yau munsha wahala ne. Ai bazan iya driving-driving ɗin nan ba a nema min driver please. Sai dai mai hankali dan ALLAH ban son mai surutu da ƙazanta”.
Dariya Amrah da Afrah da Mubeen suka sanya. Mubeen ke cewa baki son irin su Dallatu yake ko wa ma mai shegen ƙaryar nan ga yalalen haƙora”.
Itama dariyar tayi, dan ta tuna da wanda suke maganar, shine ta kora aka kawo Smart. Akwai shegen surutu da son fafa amma ba tsafta. Aiko yasha marukanta babu adadi. Haka kawai sai Smart ya zo mata a rai. Taɗan lumshe idanu da jan ajiyar zuciya, gaba ɗaya annurin fuskarta ya ɗauke. Tsam ta miƙe tabar falon suna cigaba da hirarsu bama su farga ba. Dan Ummita suka shiga bama labarin direbobin Lulun da akasha kala-kala a gidan. Tana shiga ɗakin nata da ke tsaf-tsaf yana ƙamshi mai daɗin gaske dan yana nan a yanda kowa ya sanshi da tsafta, iya Tabawa bata wasa da gyaransa saboda Lulu sam bata son ƙazanta. Abayar jikinta ta saɓule, wando da rigar data saka a ciki suka bayyana. Suma zaresu tai ta shiga wanka. Tana fitowa ta gabatar da sallar magrib da aketa yi. Alkur’ani ta ɗauka tai karatu gwargwadon abinda ya sawwaƙa kamar yanda ta saba a yanzu, kafin ta ɗora da azkar na yamma da bata samun damar nutsuwar yi sai irin iyanzu ɗin. Koda Ummita ta shigo mata da takardun ta da Laptop bata katse abinda take ba, sai ga Iya Tabawa ma da tea da Lulun kesha duk dare AA goye a bayanta. Tea ɗin ta fara ajiyewa a inda Lulun ke zama yin ayyukanta sannan ta matsa gaban gado ta sauke AA ta kwantar a hankali. An masa wankansa an masa shirin barci sai ƙamshi yake yi kamar ba dare ba. Fita sukai gaba ɗayansu suka ja mata ƙofar, dan babu kuma mai sake shigo mata kenan, itama da wahala ta sake fita in ba Daddy ne bai shigo gidan da wuri ba taje su gaisa. Kamar dai yau da suka samu baya a gida bai dawo ba.
Bayan kammala addu’ointa tsam ta miƙe ta maida komai a inda yake tare da zare abayar sallarta ta maidata a inda take ajiyewa. Doguwar riga mara nauyi da bata kai mata har ƙasa ba ta saka mara hannu. Ta ɗan rage gudun acn ɗakin saboda AA mai saurin ɗaukar mura sannan ta nufi gadon nata. Zama tai a hankali gefen da yaron yake da ga can ɗan tsakkiya tana sauke ajiyar zuciya da ɗaukar wayoyinta. Ɗan dudduba massages tayi da miss calls da akai mata ɗazun bata samu amsawa ba. Ta kira wanda zata iya ta share sauran. Sakwanin ma amsa wanda suke da muhimmanci tayi sauran ta barsu. Tana ƙoƙarin ajiye wayar kira ya shigo. Number nan ce dai da ko ta ɗaga ba’a magana tayi masifar har ta gaji, har blocking tayi amma tarasa yanda ake cigaba da kiran nata. Har ta tsinke bata daga ba, aka kuma sake kira. Tasan idan bata ɗaga ɗin ba dai ba dainawa za’ai ba koda za’a jera mata kira hamsin ne, dan haka ma take ɗagawar ta samawa kanta lafiya tunda bata san wane aljani ne ba kuma. Kamar kullum shiru anƙi ace komai, sai dai tana iya jiyo saukar numfashi da fitarsa a hankali. Itama yau sai taƙi yin magana. Haka sukai shiru kusan na mintuna uku kamar ba kuɗi ake ci ba.
“Hummm koma waye dai ALLAH ya shiryesa”. Ta faɗa cikin jin haushi da yanke kiran tana jan ƙaramin tsaki. Wayar ta jefar gefe tare da kai hannu ta gyara ma AA kwanciya, sai ta samun kanta da zubama yaron ido kamar yau ne ta saba ganinsa. Ta ja tsahon mintuna biyar tana ma yaron kallon ƙurillah tare da cakuɗa abubuwa da yawa da ke cimata zuciya. Ganin zata zurfafa tunaninta yay yawa ta sumbaci goshin yaron da sauke ajiyar zuciya mai nauyi ta masa addu’a ta gyarashi. Miƙewa tai zuwa inda take zaman aikinta ta zauna, sai da ta haɗa shayi sannan ta kunna laptop tare da rage hasken ɗakin, bakajin komai sai motsin keyboard da na ac. Ta kwashe tsahon lokaci a wajen kafin ta tashi tana faman miƙar gajiya, toilet ta shiga tai uzirirrikanta ta fito tai shirin barci ta haye gado kusa da gudan jininta ta kwanta…..
Washe gari kamar yanda ta saba da wuri tai shirin fita. Dan ma tana ta fama da AA da ya maƙale mata yau shagwaɓa yake ji, sai da Ummita ta shigo ne ta ansar mata shi ta samu ta ƙarasa gyarawa tana faɗin, “Yaro zaka gane kuranka yayeka zanyi ai a cikin watannan”.
Cikin waro idanu waje Ummita ta ce, “Kai aunty wasa kike amma dan ALLAH?”.
“Oh wasa ko zakuga wasa”.
“Kai aunty wata tara fa, baima cika cif-cif ba. Banda ma yanada kirinki da zafin nama ai bai kai a fita a barsa ba”.
“Uhm Ummita kanku fa akeji, wlhy jira kawai nake ya taka na yayesa. Tunda yana cin abincinsa ba wani ya damu da nonon bane sosai ai gara na hutar da kaina ko.”
“Mudai aunty kiyi haƙuri to ko shekara ɗaya mu cika dan ALLAH mun tuba”.
“Ummita kenan, wai baki tausayina ne ma dai ko. Da wanne zan ji?”.
“Aunty damu mana, ai mune farko kafin komai. Dan kulawar mu da ta Abbienmu itace farko”.
Shiru Lulu tai bata sake cewa komai ba. Dan a duk sanda Ummita zata ambaci Abbien AA ɗin takanji zuciyarta na mata nauyi, shiyyasa bata sakewa hirar tai nisa a kansa take basarwa. Ficewa tai a ɗakin tana faɗin, “Bari na duba Daddy zanyi breakfast a wajensa ki yi maza ki shirya kin san munada aiki yau”.
Cikin girmawa Ummitan ta amsa mata da to tare da Binta da kallo tausayi. Sosai ma’aurata ke matuƙar bata tausayi, bata taɓa ji ko labarin irin aurensun nan ba. Auren kusan shekara ɗaya da fin rabi kaɗan babu a biyu amma zaman wata ɗaya cikakken ba’a samu ba, dan ma UBANGIJI mai hikima da ya saƙa zare mai girma na azurtasu da ɗa. Tana ma kanta addu’a, amma gaskiya Lulu na ɗaya daga cikin manyan addu’ointa a kowacce rana. Fatanta ALLAH ya kawo iyakar komai ta koma wajen mijinta da ayanzu duniya ke faɗa da saurara a fanin ƙwallon ƙafa. Ita tasan duk da Lulun bata nunawa tanada damuwa sosai. Dan tasha kamata tana kallon AA kallo mai harshen damo kasancewar sa tamkar photo copy na mahaifinsa. Sannan shi kansa yaron soyayyar da take nuna masa mai kallo yasan ba tashi bace shi kaɗai harda ta Abbien nasa……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣6️⃣
……..A wajen Daddy ta karya kamar yanda ta faɗa. Sunata hirarsu cike da nishaɗi. A cikin hirar ne yake cemata yana son ya je ya ɗan huta kwana biyu da ga nan zaiga doctor ɗinsa da kuma wani business da zai yi a England. Batare da ta kawo komai a ranta ba dan harga ALLAH bata san a ina Smart yake ba yanzu, ta ce, Daddy badan ina akan gaɓar wani case ba ALLAH nima dana bika na ɗan huta kona 1week ne. Da ga nan ina son na shiga U.S ma duba wasu takarduna a gidan can”.
Da ƴar tsokana Daddy ya ce, “To ko na jiraki ne Sweetheart. Kin san fa na daɗe bamuyi tafiya tare ba ina jin kewar hakan”.
Dariya tayi da faɗin, “Daddy karka sa Naseer ya ɗauka na ƙwace masa fadarsa ta autanci fa.”
Shima darawar yay cike da nishaɗi yana faɗin, “Ai yace yanzu shi ba auta bane. AA ne Auta. Banda ƙarfin hali an taɓa ƙwace ɗan wani gida a bama wasu.”
Murmushi Lulu tai da cewa, “Nakune ai Daddy, wake da iko da shi sama da ku?”.
“A’a fa Mawaddat son kai da maida ɗan wani naka. Da haka ne ai da kema na haƙura na barma su Dada. Mahaifinsa na sane da abinsa kafin ya waiwayone kawai. Yanzu dai ki duba idan kinada dama zuwa hutun sai na jirakin, dan nima zan shiga U.S ɗin insha ALLAH. Nanny ɗinki ma ta kirani wai bata da lafiya sosai zata koma ƙasarsu Gambia tai jiyya. Amma nace ta ɗan jirani har naje sai ta wuce”
Sosai Lulu ta nuna tausayawa da mata addu’ar samun lafiya. Da ga haka suka cigaba da hira har lokacin fitarta yayi. Tare suka fito da Daddy ɗin har da Mommy data samesu itama. Ta samu Ummita na jiranta, dan haka bata ɓata lokaci ba ta ɗan tattaɓa AA da masa kiss tana jaddada ma su Amrah su ɗauki saƙon Ammah a ɗakinta idan zasu wuce kai AA ɗin yini can yau kasancewar juma’a ce duk sati can ake kaisa dama. Sun amsa mata da to ta shiga mota suka wuce….
________★
Kamar koda yaushe Ammah tayi farin cikin ganin jikan nata. Dama gashi juma’ar ƙarshen wata ce yaran gidan duk zasu zo. Shima cike da ɗokin ganinta ya maƙalƙaleta dan ya saba da kakarsa kasancewar ana kaisa. Da yaga Asma’u ma haka ya dinga zallo dan ɗan lelenta ne. Su Amrah basu jimaba suka wuce duk da ba haka Asma’u taso ba. Sai dai zasu wuce school ne dole babu yanda zasuyi. Itama yau bazataje bane saboda tun jiya tana kwance babu lafiya. Maryam kuwa tana gidan aunty Bilkisu saboda makaranta tafi mata kusa da ga can yasa tafi zama a can yanzu sai weekend ake ganinta anan gida tunda an zama ƴan jami’a bisa tsayawar Smart, da. Yaran Abba mata basa shiga jami’a sai a gidajen mazansu. Itama ganin an kawo kuɗi yasa Smart cin ƙarfin Abban da ƙyar dai ya amince ta fara. Shi kuma Smart yayi hakane saboda yasan dangin su Ahmad ƴan boko ne na gani kasheni, baya son ƴar uwarsa ta shiga cikinsu ta koma baya. Yanzu ko koba komai taci ƙarfin kusan shekara biyu kafin bikin tunda gashi yanzu tana da shekara kusan ɗaya. Bikin kuma shekara ɗaya aka saka.
Koko Amma ta fara bama AA sai ya ƙi sha ya fara bultso mata shi. Cikin dungure masa kai da faɗin, “Ɗan nema yau kuma kokon ne bazaka sha ba. Kaima dai tsurfa irin ta Babangida yana yaro duk ka iyata.”
Dariya Asma’u da ke kwance take musu. Ta ce, “Kai Ammah yayan ne yay tsurfa?”.
Ammah ta ce, “Tab har ma ana magana. Ai Hydar al’amarin sa daban ne dana kowa. Kinga tashi haɗa masa tea ko zai sha”.
“To Ammah. Amma ƙilafa baya jin yinwa ne.”
“Eh to da wannan kuma. Sai dai kum….” dai-dai nan kira ya shigo wayar Ammah ɗin. Tashi Asma’u tai ta ɗakko cikin zumuɗi take faɗin, “Ammah Yaya Hydar ne”. Murmushi itama Ammah tayi, dan haka Asma’u ta ɗaga tana gaishesa cikin farin ciki da girmamawa. Da ga can ya amsa mata da kulawa tare da tambayarta jama’ar gidan tace kowa lafiya yake. Ya tambayeta miyasa bataje makaranta ba ta sanar masa tun jiya bata da lafiya shiyyasa Ammah tace yau kar taje sai monday.”
“Okay” ya faɗa a taƙaice cikin rashin son hayaniyar nan tashi. Har zata miƙama Ammah wayar ya sake faɗin, “Kinje asibiti ne?”.
Amsa ta bashi da cewar, “A’a Aunty Mawaddat ta turomin Doctor ya dubani da dare”.
Da mamaki ya ce, “Gidan tazo?”.
“A’a Yaya ai bata iya zuwa har yanzu, ta kira Ammah ne suka gaisa shine taji Ammah namun faɗan shan magani. Tace mata ta barni bari doctor yazo ya dubani sai yay min allura idan ban son maganin ne”.
“Yayi”.
Ya faɗa a taƙaice. Da ga haka yay shiru. Ita kuma sai ta miƙama Ammah wayar. Ya gaida Ammah cike da girmamawa. Ta amsa masa da kulawa. Dariyar wasan da Asma’u kema AA ya jiyo. Ya ce, “Wake dariya haka?”.
Ammah ta ce, “Babana ne Asma’u kema wasa.
“Yau kuma anan ya kwana kenan?”.
Da ƴar dariya Ammah tace, “Banda abinka Hydar ina mai shan no-no zai kwana wani waje bada uwarsa ba. Yanzu su ƴan biyu suka kawoshi dai. Sai kuma dare sai Mubarak ko Abdull su maida shi. Sai dai nasan yanda baida da rigima kwana nan ma zai iya yi batare da ya damu ba, badai a taɓa gwadawa bane. Da har haƙurinka ya biyo bai bar komai ba shikam”.
Ɗan murmushi kawai Smart yay da ga can da faɗin, “Hummm”.
Sanin halinsa na rashin amsa komai dalla-dalla yasa Ammah fahimtar abin cewar kenan. Dan haka ta ɗora da faɗin, “Hydar baka ganin ya kamata kayi magana su taho haka nan ko ALLAH zai sa a dace komai ya daidaita, duk da dai bata iya shigowa gidan nan har yanzu kuma tana son hakan. Ko tazo sai dai ta tsaya waje shima da ƙyar ake sha dan sai ta tafi da ciwon kai. Amma ƴar albarka kullum bata gajiya sai ta kirani safe da yamma taji lafiyata. Kayan shayi da su sabulu zuwa kayan buƙata irinsu-irinsu sai dai na bama wani. Ai duk wanda yay wannan shiga tsakani na kai da iyalinka bazan yafe masa ba a wannan karon” hawaye suka cika mata ido.
Cikin rauni da sanyi Smart yay murmushin ƙarfin hali da faɗin, “Ammah dan ALLAH ni bana son kina damuwa. Komai lokaci ne ai, ALLAH dai ya bamu ikon cinye jarabawa. Wlhy ni kuma ina jin nauyin su Daddy ban san taya zan taresu da maganar nan ba. Ina ga kawai mu cigaba da zubama sarautar ALLAH ido komai zai wuce. Yanzu ya batun ganin naki likitan ne? Kodai nan zaki taho. Dan ina son itama aunty Bilkisu tazo nan ɗin saboda matsalarta, akwai wata ƙwararriyar likita anan da nake fatan insha ALLAH ta ganta za’a dace”.
“Hydar kai dai na kula baka jin kisan kuɗi sam. Wannan ƙoƙarin naka yayi akan ƴar uwarka. Amma ni dai ka barni anan ai akwai likitoci ƙwararru in sha ALLAH zasu dubani. Dan ma ka damune kawai amma ai ƙafar ba wani tanayi sosai bane yanzu tunda ka aiko min maganin nan”.
“Ammah ai lokacin abu a yisa. Da banyiba ai da bani da shi. Yanzu kuma Alhmdllh. So nake ma muyi magana da Abba dan ina son gyara gidan nan tunda naga baya son barin anguwar”.
“Tab kaima kasan mai raba Abbanku da anguwar nan ai sai dai mutuwa. Gyaran dai shi yafi kam”.
Cike da gamsuwa ya ce, “In sha ALLAHU hakan za’ayi kawai”. Da ga haka suka cigaba da hirarsu tsawon lokaci kamar yanda yakanyi duk sanda ya kira. Har sai da aka kaima su Umma suma su gaisa. Kamar ko yaushe sai da Umman ta bugi cikinsa akan komawar matarsa. Shi dai yay murmushi kawai kamar yanda yakanyi a duk sanda tai masa tambayar saboda nuna kunya. Sai dai hakan na ƙona mata zuciya da jin ƙarin tsanarsa. Cikin rashin daɗin rai ta miƙama Asma’u wayar batare da ko sallama sunyi ba. Mama ma ankai mata sun gaisa da aunty Amarya. Lokacin da ta maida ma Ammah wayar take sanar mata “Yau ma Ummah sai da ta tambayi Yaya wai yaushe zai zo ya maida Aunty Mawaddat ne? Ko baturiya zai kawo musu wannan karon?”.
Murmushi kawai Ammah tai da girgiza kai tana mai mamakin halin irin na Ummah. Tana rakata ne kawai zuwa gaɓar da take buƙatar bata amsa. Shiyyasa a yanzu take cigaba da shanye komai, dan ta gama ji a ranta da hannun Ummah a al’amarin su Smart ɗin……
________★
Tunda ya fito a prison da mahaifinsa ya sa aka kaisa jiyya ya kwanta kusan ta wata guda saboda wahalar da yaci a wajen. Da ga ƙarshe ya ɗauki amaryarsa suka wuce Mexico. Watanninsa biyu kenan sai yau ne ya dawo Nigeria. Ya murje abinsa tamkar komai bai faru ba. Sai ƙiba da ya ƙara abinsa mammokaɗewar da yay duk ta ɓace. Tafe yake cikin izzar nan tashi da ƙasaita yana faman hura hanci. Abokan cin mushen nasa ne su Hon. Nakowa sukaje tarbarsu. Sai Tajuddeen da shima baifi kwanaki uku da dawowa ƙasar ba. Shima dai ya murje abinsa kasancewar hankalinsa kwance yake akan zaman Lulu a gida. Gani yake auren ya mutu suna ɓoyewa ne. Acewarsa ta gama ɓoye-ɓoyen ya fito a ɗaura musu aure. Shiyyasa ya ajiye makaman yaƙinsa da mahaifinsa ya ɗorasa tsakaninsa da kakanninsa ya je suka dai-daita da Baba Garko. Dan ya bashi haƙuri sosai da tabbatar masa shi baya tare da mahaifin nasa, sannan bai san manufarsa akan Lulu ba. Baba Garko yaso korasa amaryarsa ta lallashesa da tausashi akan ya jawo Tajuddeen ɗin a jikinsa, hakan zai sa ya canja masa ra’ayi akan dagiyar soyayyar Lulu harma ya haƙura. Ya fahimci manufarta, dan hakan da zai yi ne kawai zai barranta halin jikan nasa da ubansa kar shima su rasashi.
A kallo ɗaya zaka ɗauka babu komai a tattare da Alh. Sulaiman ɗin sai farin ciki, nan ko zuciyar tsatstsage take da mugayen nufi musamman akan abubuwa da dama. Dan wannan karon kam ya dawo da shirinsa shiyyasa ya bada ƙafar ja baya. Acewarsa ja baya ga rago ba tsoro bane shirin faɗa ne………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣7️⃣
…….Cikin ɓacin rai abokin nasa ke kallonsa. Dan gaba ɗaya a watannin nan MM Atik ɗin ya sake birkicewa. Ɗan sauƙin da aka samu wani aiki da mahaifinsa ya haɗashi da shi ne zuwa Chaina shine dalilin ɓuyansa. Sai a watan jiya yake dawowa gida Nigeria. Abinda ya farayi shine neman Nadia. Sai dai ya taki rashin Sa’a wai tana kwance babu lafiya. Dan cikinta ya kumbura sosai tana fama da ciwon hanta da ƙoda sakamakon shaye-shaye. Ga ciki ta samu wanda taita faɗi tashin ganin ta zubar da shi amma ya gagara zuba, tayi ƙoƙarin ganin Alhaji Baita domin cikin tasan nasa ne, amma ta kasa samun kowacce irin dama. Daga ƙarshe mahaifinta ya korota da ga gidansa.
Yana gama jin abinda ke faruwa da ita a wajen yarinyar shagonta yaja tsaki da faɗin, “Mtsoww bata da wani amfani a gareni yanzu”. Da ga haka ya kaɗa kansa yay tafiyarsa. A sabon bincikensa ya gano Lulu na gida amma ta haihu, yaji baƙin ciki da jin ciwon jin kalmar haihuwar nan har ya nema susuta kansa. Dan giya ya dinga ɗorawa da cocaine yana sambatu. Da ƙyar su Asim abokinsa suka samu ya dawo dai-dai. Sai dai ya rantse yana akan bakansa sai ya mallaki Lulu koda ta ƙarfi ne dan sha’awarta zata iya kashesa. Saboda a ganin da yay mata ranar bikin ƙaddamar da ƙungiyarta sai yaji kamar ƙarya ake masa ta haihun. Dan tana nan fes da ita babu alamar wani koma baya ko tawayar haihuwa tattare da itan. Sai ma ƙyau na musamman da yaga ta ƙara masa da cikar kamala duk da yanzu dai bata shigar wando da riga ko matsatstsun kaya ta fita haka zuwai sai da abaya a sama. Wani lokacin ma da facemask, sai kuma wai yaron nan mai tashe da shi kansa yake matuƙar so wai shine drivern nan nata data aura. Wannan abu shima ya jijjigashi, ya jima yana mamaki a ransa. Amma dan ƙarfin hali har yanzu a hakan baya jin zai janye dan kullum kamar ana ƙara rura masa wutar buƙatar Lulu ne. Ko neman mata ya rage yi yanzu dan kowacce ta bar burgesa, sai ma idan ya ɗanga kina yanayi da Lulun ko idan yasha cocaine ɗinsa na faɗa masa banza wofi ya jajubeki, yana dawowa hayyacinsa kuma a ƙare da bala’i maybe ma ki samu tsabar duka…
Ko sau ɗaya bai kula Asim ɗin dake fece shi game da nacinsa akan Lulun ba. Sai ma miƙewa da yay yayi shigewarsa toilet ya bar Asim ɗin na cigaba da masa hayaniya….
__________★
Sosai abubuwa sukama Lulun yawan da har tace bazata bi Daddy ba ta fasa. Lallaɓata ya dinga yi har taso fara tsarguwa sannan ya taƙaita. Daga ƙarshe dai ta ce zataje ɗin kodan takardun nan da take son ɗakkowar. Taje gidan Uncle Yousuf suke maganar da aunty Saliha. Murmushi kawai aunty Saliha tayi dan tasan da tafiyar dama a bakin Uncle Yousuf da baya ƙasar. Wasu abubuwa ta haɗa ma Lulu wai na gyaran jiki. Bata kawo komai ba ta amsa dan yanzu ta dage da irin abubuwan gargajiyar nan ganin sun amshi fatarta da ƙyau. Ga kamshin da yanzu ya kama jijinta kuma duk dai irin haɗin su khumra data raina a da ne. Koda ta dawo gida batayi wasa da su ba, yayinda Mommy ma a kaikaice take ta bata nata sirrikan. Hatta da iya Tabawa ba’a barta a baya ba. Da ga ita sai AA zata wuce. Taso suje da Ummita amma Daddy yace ta bari sai da ga baya, idan ma harda iya Tabawa take so duk zai haɗo mata. Dariya tayi da faɗin, “Haba Daddy sai kace wadda zataje zama. Su bari kawai mu dawo danni ko Aliyu da zaku bari a gida zan barsa”.
“A’a bazai yiwu ba kije da shi shima ya huta. Tafiya babu abokina ai bazai mun daɗi ba”. Yay maganar yana lakace hancin AA dake tsale-tsalle a jikinsa. Murmushi kawai Lulu tayi daga haka suka cigaba da shirinsu musamman ma shi AA da komai sai an masa.
*_UK LONDON_*
Tafe yake a nutse kan ƙafafuwan sa. Da ka gansa kaga tsayayyen mutum mai cike da jatumta da lafiyar gaɓai. A komai nashi babu hayaniya babu ɗagawa duk da wasu kan fassara shiru-shirunsa da girman kai tun bai zama wani ba. A duk sanda yake da uzuri na fita ya kanfi buƙatar takawa da ƙafarsa in har wajen da yake son zuwan babu nisa. Kamar dai yau da ya fita zuwa shopping na ƴan abubuwan buƙatarsa. Ya riga da ya kai wani matsayi a yanzu da fuskarsa ta zama ba ɓoyayya ba musamman a cikin birnin London. Hakan yasa a duk sanda yake da buƙatar irin fitar nan yakan sakaya fuskarsa da abinda zai ɓadda masa kamanni. Kamar dai yau, ya saka facemask da glasses, ya kuma ɗaura p-cap duk dai cikin son kaucema idanun jama’a dan yaje ya dawo batare da kowa ya damesa ba. Alhmdllh har ko yaje ya dawo babu wanda ya ganesan, garama a cikin mall ɗin da yaje biyan kuɗi kasancewar dokace sai anga fuskarka da yaja nurse mask ɗin ƙasa mai cire kuɗin ɗin ta wani zaro ido bakinta a washe zata ambaci sunansa yay mata murmushi da mata alama zip abaki. Dole tai shiru amma murmushi da farin ciki yaƙi barin fuskarta, har da ɗan leƙensa da zai wuce, sai da ya fice gaba ɗaya take faɗama sauran ƴan uwanta da ke wajen harda masu cewa basu yarda ba. Wasu kuma suka biyo bayansa. Ya riga ya zargi za’a iya yin hakan dama sai yana fitowa ya canja hanya. Wannan yasa suka sake tabbatar mata basu yarda ba. Ba komai ya sasu jin basu yardan ba sai dan mall ɗin nasu ƙarami ne, a ganinsu Smart Mawashi yafi ƙarfin zuwa nan yin shopping. Irinsu ma sunfi son yin online shopping a manyan mall ai.
Ɗayan hannunsa da babu kaya ya fiddo da ga cikin aljihu wandonsa ya saka security ɗin ƙofar. Sai da computer ta ambaci sunansa sannan ƙofar ta buɗe kanta a hankali. Numfashi ya ɗan furzar yana tura kansa cikin gidan bakinsa da sallama duk da yasan shi kaɗansa ne a gidan nasa. Tuni ya samu canjin wajen zama. A inda yake nan gida ne shi kaɗai a ciki madaidaici mai ƙyau da tsarin birgewa, dan yana ɗauke da abubuwan more rayuwa da ɗan adam kan buƙata koda da sha’awa ne. Ya cire takalmansa a inda yake ajiyewa yasa slippers na zaman gida, tare da hanging rigar sanyinsa sannan ya ƙarasa shiga. Ya ɗan bi falon da kallo ganin fitila a kunne ga wani baƙon ƙamshi, sai dai bai kawo komai a ransa ba ya ɗan ɗage kafaɗu da taɓe bakinsa tunda yasan dai bayan Uncle Yousuf da yasan security ɗin gidan babu wanda zai iya shigo masa, sai ko Ahmad, maybe ya manta ne da zai fita bai kashe fitilan ba. Kayan shopping ɗin nasa ya kai duk inda ya dace sannan ya nufi bedroom ɗinsa hannunsa riƙe da jacket ɗinsa da ya zare ya ɗan sagalota a kafaɗa. Tafiya yake a hankali kamar cikin kasala da gajiya yana latsa waya da alama akwai abinda yake sonyi ko kira. Cikin rashin maida hankali ya tura ƙofar ɗakin da ƙafa ya shiga tare da sake turata da ƙafa ya rufe. Dai-dai nan take fitowa daga Bathroom sanye cikin rigar wanka pink da tazo da abinta. Sosai gabanta ya faɗi da ganin mutum ya shigo mata kai tsaye a inda batai tunanin ganin wani ba, duk da tun shigarta bathroom ɗin ta shiga halin tsarguwa amma ta dake. A bedroom komai need yake babu tarkace babu abinda aka bari a waje da zaisa ka zargin akwai mai amfani da ɗakin sai a toilet ɗin ne, sai dai wani tunani da yazo mata ya sata gamsuwa tai wankanta hankali a kwance.
“Who are you Man?!”.
Ta faɗa cikin faɗa da son dake razanar da tayi. Shi kansa gabansa ne ya faɗi, ya ɗago da sauri dan yasan bai bar kowa a gidansa ba shi dai, amma sai ga muryar mace a tsakkiyar kansa a cikin ɗakin barcinsa bama falo ba. A karo na biyu ƙirjinsa yay wata irin jijjiga ganin wadda bai zato ko tsammani ba, wayarsa da ke neman suɓuce masa a hannu yay saurin damƙewa, sai kuma ya ɗan ja baya kaɗan gannin tayo kansa da masifa hannunta ɗauke da wani deco.. da ke ajiye a bedside drawer ɗinsa. Duk da yana a cikin yanayin ruɗani sai da ta so bashi dariya amma ya dake, yo abinda ta ɗakko ɗin ko buga masa tayi mizai ji duk da glass ne. Tana gab da zuwa ina yake ya ce, “Please Relax Ladyy”.
Cak taja ta tsaya zuciyarta na harbawa da masifar ƙarfi dan ko’a magagin barci wannan deep voice ɗin bazata layance mata ba. Cikin rawar lips da ta murya ta furta, “Aliyu!”.
Idanu kawai ya zuba mata ta cikin glasses ɗinsa na kusan sakanni talatin, kafin a hankali ya kai hannu yay ƙasa da mask ɗin fuskarsa tare da zare glasses ɗin. Idanun ya lumshe a hankali tare da sake buɗewa yana mai kamo gefen lips ɗinsa da haƙori. Kallon nasa da yanda gaba ɗaya ya canja fiye da ganin datai masa a lokacin haihuwar AA a Canada ya sata jin kamar jiri na neman kwasarta zuwa ƙasa ne ma. Shima yana jin fiye da abinda take ji ɗin, sai dai ƴan mazan a tsaye suke banda a ƙwayar idanunsa bata iya hango komai da zata iya bama fassara. Son tabbatar da ba aljana bace ko mafarkin da ya saba harta fara masa gizo ya sashi kauda idanunsa a kanta ya fara waige-waige. A saman gadonsa ya hango abinda yake neman a kwance yana barcinsa da alama ya gaji dan yayi wani baje-baje da ƴan kafafu da hannuwa yana zuƙar iskar sabuwar ƙasar Babansa da fesarwa cikin kwanciyar hankali. Karo na farko ya saki murmushi ganin wanda ya bari a jinjiri ya fara zama mutum, dan girman jikin AA yafi watanninsa yawa kasancewar ya ɗakko har tsawo irin na gida. Duk wanda ya kallesa yasan su ɗin jini ɗaya ne dan kamaninsa sun sake bayyana kansu matuƙa a tattare da yaron. Lulu da ke jin wani yamm-yamm kamar zata zube ƙasa a hankali ta furzar da iska mai nauyi tare da jan jikinta baya a hankali ta koma bakin gado ta zauna cikin dafe kai. Wato ta fahimci Daddy da Uncle Yousuf wayo sukai mata kenan kawai. Shiyyasa taita fama da shi su fara zuwa U.S amma ya dage su fara zuwa UK yana da abinda zaiyi mai muhimmanci. Takun sawayensa ya sata kallonsa ta gefen ido, ganin kamar inda take yayo ya sata ɗagowa sosai tana masa kallo mai kama da harara. Sai kawai ya basar ya wuceta zuwa inda yaronsa yake………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣8️⃣
……..Tattaɓa shi ya shigayi idanunsa na cika da kwalla, sai kuma ya rankwafa da ƙyau daga zaunen da ya kai ya manna masa kiss a goshinsa da kumatu duk biyu. Kamar AA yasan mi ake ya wani juya abinsa ya kwanto a hannunsa. Murmushi yay mai kama da ƴar dariya, sai shima kawai ya kai kishin giɗe ya rungumesa a jikinsa sosai yana sakin ajiyar zuciya masu nauyi da shafa lallausar sumar kan yaron da Lulu ta hana a aske, sai gyaran fuska ake masa. Yaja kusan mintuna biyu a haka kafin ya ɗago idanunsa ya dubi Lulu da ke satar kallonsu. Kanta tai saurin maidawa gefe cikin taɓe fuska. A karo na farko yay magana cikin ɗan sakin murmushi. “Irin wannan bazata haka Madam?”.
Mikewa tai tamkar bata jisa ba zuwa inda akwatin kayansu yake, dan ɗaya ta ɗakko jal ita da AA, kayansa ma sunfi yawa dan nata basu wuci kala uku ba sai kayan barci. Sai da ta zuge zip ɗin tana ƙoƙarin ɗaukar kaya sannan ta bashi amsa da “Sai yanzu kasan da ni?”. Bata jira amsarsa ba ta wuce closed ɗinsa hannunta riƙe da kayan data ɗauka taja labulen da aka sa a wajen wai dan karya kalleta.
Da ƙyar ya iya danne dariyarsa yana mai lumshe idanu, ya dai fahimci kishi ake da AA ɗinsa kenan. Mintuna kaɗan ta fito sanye da wando da riga marasa nauyi, sai dai yanda suka bi jikinta da fidda mata surarta fes ya saka zuciyar ƴan maza motsawa. Ga Lulu hakan normal ne, ita batayine dan wani birge miji ba, tun fil azal wannan shine dressing nata. Batare data kallesa ba ta wuce gaban mirror ɗinsa dake cike da turarruka da mayukan gyaran gashi sai abinda ba’a rasa ba. Gashinta taƙe ƙoƙarin tifkewa. Kwanciya ya gyarama AA tare da miƙewa, dai-dai tana tattare gashin cikin hannunta bayan ta zare ribbon ɗin data ɗaurosa da shi sukai ido huɗu da shi a bayanta. Yay wani tsaiwar ƙasaita irin na isassun maza yana kallonta da mayatattun idanun nan nasa. Sosai ta ƙara jin ƙirjinta ya motsa, tai azamar janye idanunta tamkar bata ganshi ba. Idanun ya rufe ya buɗe a lokaci guda yana ɗan ƙara matsawa jikinta daf ya mata runfa, sai kuma ya ƙarasa rungumeta a hankali tare da ɗaura kansa a kafaɗarta. A tare suke ja numfashi da sauke ajiyar zuciya mai nauyi. Yanda yake wani bin wuyanta da shinshina idanunsa a lumshe ya sata jin tana neman zubewa a ƙasa, saurin riƙo hannayensa duk biyu da ke zagaye da ita a saman cikinta tai, hakan ya sakashi sake ƙanƙameta tsam-tsam kamar za’a ƙwace masa ita ya wani busa mata numfashi a cikin kunne….
Harga ALLAH bazata iya ɗaukar wannan salon nasa ba, dan haka tai ƙoƙarin jan jikinta da saurin faɗin, “Wai nikam minene haka?” cikin rawar murya data lips. A cikin kunnenta ya raɗa mata “Saƙon barka da zuwa mana. Haka ya kamata ki tarbi mijinki _My Final Choice_”.
Kanta ta matsar gefe tana taune lip ɗinta na ƙasa, cike da basarwar nan tata cikin son janye jikinta ta ce, “Kama nemo Final Choice ɗin naka bana son iyayi”.
Sake ruƙota yay sosai yana murmushi. Idanunsa ƙyar a kanta ta cikin mirror ɗin ya ce, “Kowa yasan na nemo abita ai tuni. Dan duniya duk ta san Mawaddatan’warahmah ce Heart controller ɗin Aliyu Hydar Mika’il Mawashi”.
“Kai dai ka sani”.
Ta faɗa tana janye jikinta a nashi. Bai hanata ba ya saketa tare da harɗe hannayensa a ƙirji. Kallonsa tayi ta ɗauke kai da rusinar da idanunta. A hankali ta ce, “Malam matsamin na wuce”. Dan ya tsare mata ko ina. Bai matsa ɗin ba, bai kuma daina kallonta sama da ƙasa ba. Kallo irin mai haka mutum sukuni ɗin nan da ji iska ma na maka wahalar shaƙa. Ƙoƙarin raɓasa tayi ya tare, ta sake komawa ɗayan ɓangaren, nan ma ya tare, ta koma tsakkiya nan ma ya tare. Sai kawai ta zabga masa harara tana tunzura baki. Hannayensa ya warware da ƴar murmushi har sannan a fuskarsa ya ɗan matsota, baya ta matsa ta manne da mirrorn. Shima sai ya dafe hannayensa a mirror ɗin ta gefe da gefenta ta koma tsakkiyarsa, ya ranƙwafo sosai yana busa mata numfashinsa a fuska. Ga son su haɗa idanu da yake faman yi. Cikin daburcewa ta furta “Aliyu!”.
“Uhmyim Mawaddat!”.
Ya amsa mata kafin ma ta gama rufe bakinta, sai taji ma ta sake daburcewa dan yanda yay kiran sunan nata da amsawa acan ƙasan maƙoshi da busa mata numfashin yasa ƙafafunta ma suka fara rawar son kasa ɗaukarta. Ɗago idanunta da suka tara ƙwallar da ita kanta bata san dalili ba tayi, hakan ya bashi damar ɗaura lips ɗinsa akan nata kamar dama abinda yay target kenan. Kafin tai wani yunƙuri ya tallafi kanta da ƙyau da hannun damarsa, ɗaya hannun kuma ya saukesa akan bayanta. Sam bata da wani sauran ƙarfin yin wani yunƙuri, dole ta haƙura dan tasan wani buyaginta bazai sa ya fasa ba in dai shi ne, sannan ita kanta kawai ƙarfin hali ne tana buƙatar mijinta. Jin tsaiwar na neman gagararsu yay ƙoƙarin tattarota zai ɗaga. Da sauri ta tattaro nata ɗan hankalin waje guda itama ta kai masa ɗan duka a gefen cikinsa….
“Ouch!”.
Ya faɗa yana sakinta yana dafe wajen. Sai kuma hankalinta ya tashi ganin yanda ya duƙe, cikin rikicewa ta ruƙo hannunsa dake riƙe da inda ta bugesan duk da dai ita tasan kaɗan ta masa. Muryarta har rawa take wajen faɗin, “Please kayi haƙuri ALLAH ban san zai maka zafi ba, wayyo ni”.
Sake langaɓewa Smart yay kamar gaske, ta kamashi ta jinginar da mirror ɗin tare da ɗan daga rigarsa tasa hannunta a wajen tana murza masa a hankali. Sake langaɓe murya yay yana faɗin, “Wayyo zafi Ammah kizo ta targaɗa miki ni”. Harga ALLAH Lulu ta ɗauka da gaske yake, dan haka ta sake ruɗewa har idanunta na tara ƙwalla, duk yanda yaso riƙe dariyarsa hakan na neman gagara, dole ya saketa dai-dai tana kwantar masa da kai a kafaɗarta.
Galala tai tana kallonsa ga hawayen da suka cika mata ido na neman fara zubowa. Cikin son danne dariyar da ke ƙara tunƙuro masa ya ce, “Dama haka kika damu da Aliyu? Madam!”.
Hararesa ta ballara masa da raɓawa ta gefensa ta wuce tana jan ƙafa da ƙyar dan ji take tamkar zata zube ƙasa ma. Shima sai yaja nasa jikin yana murmushi zuwa ƴar ƙyaƙyƙyawar kujerar dake gefe da ɗan table mara tudu dai-dai ita da zaka iya miƙe ƙafa a kansa ya zauna yana sauke numfashi da ƙaramar dariya. Sai da ya bada kusan mintuna biyu hankalinsa ya dawo jikinsa sannan ya tashi zaune da ga kwantar da bayansa da yay ya buɗe idanunsa a kanta. Tama kwance kusa da AA ne idanunta a lumshe ta wani dunƙule jikinta waje guda kamar wata baby. Ƙaramin murmushi ya saki da miƙewa ya fara zame kayan jikinsa da faɗin, “Ya kamata ki fara cin abinci kafin ki kwanta barcin ko”.
Shiru kamar bazata amsa masa ba, sai can a takaice ta ce, “Ba buƙata”.
Bai sake cemata komai ba ya nufi bathroom. Da kallo ta bisa, sai kuma rashin sake cewarsa koman ya bata haushi ta wani tura baki da hararar bayansa tana murguɗawa ta maida idanunta ta rufe. Ya ɗan jima kafin ya fito ɗaure da towel yana goge jiki da ƙarami. Kai tsaye wayarsa da ke ring ya nufa yana ɗan yamutsa fuska da kallon agogo. Bai niyyar ɗauka ba, sai dai ganin Ahmad ne ya sashi ɗagawar tare da ɗaukar bluetooth ya manna a kunnensa ya cigaba da abinda ke gabansa da alama Ahmad ɗin yake saurare.
“Ka kira dai kayi gulma ɗan sa ido”.
Dariya Ahmad ɗin ya kwashe da shi da ga can. Ya ce, “Ai kai dama ba’a maka abin arziƙi. Ni yarona na kira naji yaya yazo bai jigataba dai ko?”.
“Ga shi nan na samesa yana kwasar barci dan sun shigo gidan na fita. Yaya kun gama da mutanen?”.
“Har yanzu dai ana cuɗawa, naga sun ɗauki burin duniya sun ɗaurama wajen. Amma dai za’a dai-daita in sha ALLAH dan naga da Yaya yace zamu haƙura kuma kamar sun damu.”
“Oh kuma dai?”.
“Ai kasan dama irin wannan matsalar ba daga masu kayan bane masu sayarwar ne”.
A hankali ya ɗan furzar da iska da faɗin, “To duk yanda kukai dai?. Ya batun wancan aiki? Yaushe ne kuma shigowar taka?”
“Ai maybe ma na fasa, dan business ɗin bai faɗa ba har yanzu, kasan abinda ma lura da shi komai suna fara yinsa ne a tsare kafin su sakeshi a kasuwa, amma dai shi guy ɗin nan ya tabbatar min zai haɗani da ogan nasu saboda nace masa ni dila ne, sannan pharmacy ɗin nan ya kamata aikinmu ya fara ta kansu dan na sake zuwa da takardar nan still sun saida min jiya. Kaga tabbacin maganarka kenan ta fito”
“Hummm aina faɗa maka dama. Sai dai inaga kafin hakan ya kamata musan mai pharmacy ɗin. Sai Companyn da yafi kawo musu kaya. Dan ina son mu fara da mutuminka ne”
“Uhm wannan ma tunani ne mai ƙyau, sai dai kuma kamar abin zai mana wahala nake ga. Kasan fa kai ka fini dabaru ta irin waɗan nan fannin”.
Murmushi Smart yayi yana ɗan lumshe ido. Cikin ɗan furzar da iska yace, “Kaima zaka iya Ahmad. Ka nutsu na maka bayani, yaro zamu samar da zai nema aiki a wajen, ta silar yaron ma zamu samu abinda bamu hasaso ba ma. Plan a kenan, idan wannan zai ja mana lokaci plan b muja yaro ɗaya dake pharmacy ɗin a jiki, ta hanyar masa alkairi kasan dai yanda mutanenmu suka ɓaci da wannan karɓar na goran, a cikin biyun nan zamu dace da ɗaya”.
“Yess boss na fahimce ka, kuma tabbas wannan dabaran yayi, shiyyasa nake sonka”.
“Ɗan iska waye boss ɗin naka?”.
Dariya Ahmad ya sanya da faɗin, “Kai mana. Zanyi ƙoƙarin nan daga nan zuwa next week, Dan Cameroon ma nake son zuwa kawo shanun nan dai. Ya kamata ka shigo ayi harkar nan da kai ALLAH, dan na hango za’a samu alkairi a ciki.”
“ALLAH mutumina! Kaifa nasan baka wasa dama da harkar ƴan canji. Yanzu yaya za’ayi?”.
Cikin dariya ya ce, “Masheranci, kaima naga ai bawasan kake da su ba. Muyi magana kawai idan ka samu time, yanzu karna shiga lokacin Madam tana amaryarta. A huta lafiya tsohon ango”.
Kafin Smart yace wani abu ya yanke kiran. Ya ɗan lumshe ido da girgiza kansa yana furzar da iska. Yana ƙoƙarin cire bluetooth ɗin idonsa ya sauka akan Lulu ta mirror da ke kallonsa………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 3️⃣9️⃣
…….Sai dai yana waigawa ta rufe idanun ita a dole barci take. Nasa idanun ya rufe da sakin guntun murmushi ya ƙarasa shiryawa ya miƙe. Wando yasa 3quater da ƴar riga armless yasa turare. Baice da ita komai ba ya fita domin duba mima zai bata taci ne duk da yasan halinta bawai ta damu da abinci bane. Ganin babu wani abinda zata iya so sai kawai yay mata order na gasashen kifi da abinda yasan zata iya so. Cikin abinda baifi mintuna ashirin da biyar ba aka danna bell ɗin gidan. Tashi yay zuwa ƙofar dan yasan abinda yay order ne aka kawo. Shi ɗinne kuwa. Mai kawo saƙo ɗin na ganin shine ya wani washe baki, cike da zumuɗi da farin ciki ya ce, “Smart Mawashi”.
Murmushi Smart yay masa. Shi kuma ya zaro wayarsa yace Please ya bashi dama suyi hoto ɗaya. Kai ya jinjina masa alamar babu damuwa. Ya gyara sukayi sai farin ciki yake yi. Shi kuma ya amsa kayan ya koma ciki. A falon ya ajiyesu ya nufi bedroom ɗin…..
*_NIGERIA_*
Kamar yanda ta saba a ƙarshen kowane wata take sake ƙulla silin zare ɗaya a jikin battar da malamin ya bata game da asirin da taima Smart da Lulu. Yau ma cikin nishaɗinta ta jawo battar hannunta riƙe da farin zaren kirtani tana ɗan raira waƙarta ta barmani coge alamar dai tana a cikin nishaɗi. Dan bayan Aunty Amarya da Ammah ta sanar mawa babu wanda yasan yau Lulu ta koma wajen mijinta a gidan.. Wani irin kwance-kwance ƙirjinta yay ya yanka lokacin da take jawo battar idanunta ƙyar akan zararrikan data ɗaura zube ƙasa a warware. Battar ta tukunyar ƙasa ƴar ƙarama ta wani tsage daga sama har ƙasa. Tana ɗagata ta rabe biyu tsokokin nama biyu da suka wani tsotse a waje guda tsire da allurai suka zube a ƙasa. Ƙara ta daddage ta fasa na tsananin fita hayyaci da tashin hankali batare data farga da ɓaranɓaramar da take neman yi ba. Su Huwaila dake falo suna kallone farkon shiga a ɗakin nata a gigice. Ganinta kwance wanwar a ƙasa babu numfashi ga wata ƴar tukunya-tukunyar tsafi zube a ƙasa harda allurai a jikin tsokar nama ya sasu suma fasa ƙararar data ankarar da su Ammah. Kusan a tare suka afko ɗakin tare da gayyar yaran gidan. Babu wanda idonsa bai gane masa wannan tarkacen tukunya ba idan ya shigo, har Abba da ya shigo a ƙarshe dalilin kiran da Salis yaje yay masa akan tarkacen ya fara sauke ido kafin Ummah dake kwance wanwar ana sheƙa mata ruwa amma babu alamar numfashi tattare da ita.
Wani irin harbawa ƙirjinsa yayi tare da jin kansa ya sara. Yana sake maida idonsa akan Ummah ya ga ta koma masa wata irin mummunar hallita. Da sauri ya kauda kansa yana mai ambaton sunan ALLAH. Yanda yay baya zai faɗi sai da Ammah ta tarosa tana faɗin, “Ya Salam Abbansu yi ahankali”.
Hannun Ammahn ya riƙe yana jujjuya mata kai, muryarsa na rawa ya ce, “Hafsat fiddani a ɗakin nan kaina zai fashe”.
Furucin Abba yasa gaba ɗaya hankalin sauran yaran da su Aunty Amarya dawowa kansa. Sai kuma hankalin kowa ya sake tashi ganin halin da Abba ke a ciki. Amma mi abin mamaki yana fitowa ya saki wata nannauyar ajiyar zuciya da sakin kan. Kallonsa Ammah tai da faɗin, “Yaya dai Abbansu?”.
Kamar bashi ya gama cewa kansa kamar zai fashe ba ya ce, “Wlhy Hafsat kinji kuma ya saki kamar ba’ayi komai ba.” Sosai abin ya ɗaure kanta. Bata gama fita a mamaki ba kuma sai ga yaran na fitowa da ɗaɗɗaya hannayensu dafe da kansu. Wasu ma a guje suke faɗin, “Dodo! Dodo!!”. Cikin ƙanƙanin lokaci gida ya gama rikicewa. Kowa ya fito a ɗakin Ummah, da kuma sun fito sai su jisu sakawai kamar an zare musu komai. Umma da hayaniyarsu ta sakata farfaɗowa cikin tashin hankali tabisu da kallo ganin yanda suke fita a guje. Ganin babu kowa sai taga damace ta sameta ta tattare kayan nan. Da sauri ta tattarasu jikinta na mazari ta ɗaure a ɗan kwali ta tura ƙarƙashin gadonta. Sannan ta fito cikin ƙarfin hali. Tana sakko ƙafarta waje yaran suka shiga yanka ihu suna kwasa da gudu zuwa ɗakunan iyayensu da faɗin, “Wayyo Umma ta zama dodo! Ummah ta zama dodo!”. Ba yaran kawai ba sai ga su Aunty Amarya suma duk sun rufta ɗakunansu. Abba ma har tuntuɓe yake na barin wajen sai Ammah ce ke kallonta da ambaton addu’oi a bakinta. Dan itama kam yanzu a wata irin mummunar siffa mara ƙyan gani tane kallon Ummahn. A nutse ta nufi nata ɗakin itama aka bar Umma ita ɗaya a tsakar gida cikin tashin hankali da mamaki. Sai kallon jikinta take taga minene sukema gudu amma bataga komai ba. A take jikin nata ya kama rawa. Ɗakinta ta koma ta jajibi waya tai kiran Hajiya Naqiba….
*_★UK★_*
Cikin mamaki Smart ke kallon Lulu da ta buɗe gasashen kifin ta maida ta rufe da sauri fuskarta a ɗan yamutse. Dan shi dai a sanin da yay mata tana son kifi sosai. Shi kam baya so, dan ko a yanzu haka dauriyar shaƙar ƙamshinsa kawai yake yi. Da farko yayi tunanin halin nata ne ya motsa, sai ya so ɗauke kansa. Amma ganin yanda ta tura baki da faɗin, “Nifa bana cin kifi yanzu” ya sakashi zuba mata idanunsan nan.
Cike da shagwaɓa ta ce, “Ni ka daina kallona da wannan idanun”. Ƙaramin murmushi yayi da janye idanun nasa, da kulawa ya furta, “Yaushe kika daina cin kifi kuma Madam?”.
Harararsa tai saboda Madam ɗin da ya kirata da shi, sai ya riƙe kunnuwansa alamar sorry. Mikewa tai tana ƙara tura bakin. Hannunta ya riƙo da sauri dan yasan kaɗan daga aikinta tace zata koma bedroom ɗin da da ƙyar ya samu ta fito. Saman cinyarsa ya zaunar da ita, cikin lallashi kamar wata ƴar yarinya ya ce, “Faɗa min yaushe kika daina cin kifi?”.
A ɗan tunzure ta ce, “Da cikin ɗanka”.
“Woow really?!”.
Kanta kawai ta jinjina masa da yunƙurin tashi ya hanata damar hakan yana dariya ƙasa-ƙasa da faɗin, “Oh oh like father like son. Babie luv anya akwai wanda ya kaini sa’ar nasara a ƴakin ƙasa da ƙasa kuwa?”.
“Kamar ya?”.
Ta faɗa tana kallonsa a karo na farko. Gira ya ɗage mata tare da kwantar da kasa a kirjinta ya ce, “Aliyu ɗan Aliyu a suna. Aliyu ɗan Aliyu a kamanni. Aliyu ɗan Aliyu a hallaya. Ya kamata ki bani Award na gwarzon shekara ALLAH kuwa.”
Ƙoƙarin ture masa kai take ya riƙe hannun, cikin mamaki ta ce, “Wai dan ALLAH yaushe ka lalace haka Aliyu? Ko abinda zama cikin turawan ya koya maka kenan kai?”.
Idanunta da suka canja launi ya ɗago yana mata wani irin narkakken kallon da ya sanya jininta da tsigar jikinta yamutsawa a lokaci guda. Cikin motsa lips ɗinsa a hankali ya ce, “Kece kika lalatani fa Mawaddatan’warahmah.”
Da sauri ta waro manyan idanunta a cikin narkakkun nashi. “Ta yaya?”.
Bakinsa ya kai dai-dai kunnenta ya raɗa mata maganar data sakata jin inama kasa ta tsage ta shige kawai. Dan a take ta wani daburce ta shiga kai masa ƙananun duka a ƙirji. Hannayen ya shiga ƙoƙarin riƙewa yana dariya. Har sai da ta kai shi da kaiwa kwance a kujerar, bata barshi ba ta bisa tana a saman jikinsa ta cigaba da mintsininsa shi kuma yana tarewa da faɗin, “Wayyo fatana da zafi fa ban san mugunta baby luv”. Yanda taga yana ɓata fuska alamar zafin dai yake ji da gaske duk da bada wani ƙarfi take masa ba ya sata fara dariyar itama. Abu mai wahala ga Lulu kenan, kaga tana dariya haka tab ɗin, ai ko murmushi sai a inda taso ga kuma wanda taso. Gaba ɗaya ma sai ya shagala ma shi yana kallonta tamkar ya samu television.
Dariyar ta daina yi ganin yanda ya zuba mata mayatattun idanun nasa da gaba ɗaya suka canja launi da ƙanƙancewa, sai dai murmushi bai bar fuskarta ba, ta ɗan lakace masa hanci da ɗage gira ta ce, “Kallon fa?!”
Idanun ya lumshe a hankali da sake buɗesu a kanta, “Dariya na miki matukar ƙyau my heartbeat”. Ya faɗa cikin wata irin murya mai laushi da sanyi. Samun kanta tai da lumshe nata idanun itama tana ɗan kauda fuskarta gefe da ƙoƙarin sauka a jikin nasa. Hannunta ya riƙo ya dawo da ita ta kwanto jikinsa fiye da farko, fuskarsu gab-gab da juna suna musayar numfashi. A hankali ya sake faɗin, “Kada ki sake barina dan ALLAH. Ina azabtuwa matuƙa Mawaddatan’warahmah. Wlhy kece farin cikin Aliyu, kece bugun zuciyarsa, kece sanyin idaniyarsa, bayan mahaifiyata bana jin na taɓa jin wata mace a cikin jinin jikina da komai na sama da ke. Ki bani dama koda ƴar karama ce domin tabbatar miki da hakan Pleassseee!”.
Wani irin luuuu tayi da idanunta ta lumshesu, sai kuma ta sake buɗesu a kansa. Cike da basarwa ta kai yatsanta saman lips ɗinsa ta fara zagayawa. “Dama kai ɗan ƙwallo ne?”. Ta faɗa cikin basar da zantukansa. Idanunsa da ke rufe ya buɗe a kanta. Jan ajinta na sake rikita masa lissafin rayuwa, ya ce, “Humm!”.
Gira ta ɗaga masa kaɗan tana wani cije lips da jan hancinsa. “Miye wani Hummm amsa nake so da baki?”.
Kauda fuskar tashi ya ɗan yi gefe yana murmushi, kafin ya sake maido idanunsa a kanta da ɗan juyasu alamar tunani. Sai kuma ya ɗan ɗage kafaɗu da taɓe baki kaɗan ya furta, “Tun ina yaro ma”.
“Uhhyim! Shine ka zama kuma driver?”.
“Ƙaddarata ce wannan”.
“Bani labari to”.
Cikin ɗan ɓata fuska ya ce, “Ba yau ba amma?”.
“Miyasa?.”
“Saboda ina da abinda yafi labarin muhimmanci. Ango fa nake ki tausayawa min? Niba ɗan jarida ba na ƙare da bada labari haba ai ace min ma shakatafi”.
Kalmar shakatafin ta bata dariya, dan haka ta murmusa har haƙoranta na bayyana. Ta ce, “Miye shakatafin? Ni Bama gane manya-manyan hausar nan naka suna yin girma da yawa”.
“Oh kefa na manta rabi da rabi ce baki cika bahaus”.
“Kai ka rabani ɗin ko?”.
“Inba ni ɗin ba waya isa kaiwa ga wannan aikin”. Ya faɗa cikin fassara maganar tata da wata siga daban.
“Kai kana da matsala ba’a hirar arziƙi da kai. Sakeni naci abinci na fara jin yunwa”.
“Sorry na daina ayi hirar arziƙin. Abinci kam nan kawai ya isheki ƙoshi yau ai”. Ya ƙare maganar da nuna lips ɗinsa.
“Lips ɗinne kuma ya zama abinci?”.
“Sosai kuwa, kona gwada miki”.
“A’a na yafe girmana bai kai can ba”. Ta faɗa tana ƙoƙarin sauka a jikinsa………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣0️⃣
…….Ƙaramar dariya yayi da ɗage gira sama ya ce, “Nima naga alama ƴar ƙanwata babu abinda ta sani sai cin abinci da barci”. Ya ƙare maganar da lakace mata hanci.
Hannunsa ta buge da sake yunƙurin tashi tana faɗin, “ALLAH dai ya shiryaka kai kam”.
Sakin nata yay yana dariya da tashi zaune shima cike da shaƙiyanci.
“Miye na dariyar to”.
“A’a babu komai ƴar ƙararrama, ai ko cikin AA ma a ruwan madara kika sha ni shaida ne.”
“Kaji da shi dai. Fitinanne”.
“Kema zaki zama fitinanniyar”.
“ALLAH ya tasreni wlhy”.
“Sai dai na gaba wannan dai ya faru tunda ga AA a duniya”.
Da sauri ta miƙe cikin ɗage kai tana faɗin, “Oh kama tunamin, yaron nan zai iya tashi ya ce zai sakko wlhy”.
Miƙewar yay shima da cewa, “Yi zamanki ina zuwa, bari na duba shi.” bata Musa masa ba ta koma ta zauna. Sai dai har ya gama haye ɗan steps ɗin hanyar bedroom ɗin nasa tana binsa da kallo, sai da ya shige ta sauke nannauyar ajiyar zuciya da lumshe idanu tana sakin wani ɗan murmushi mai sanyi. Babu jimawa sai gashi ya dawo ɗauke da AA kuwa a hannu, sai zillewa yaron yake da ɓata fuska irin na ƙiwa, shi adole bai sanshi ba. Yana ganin Lulu ya wani zabura wajenta yana ɓare baki. Dole ta amshesa dan ya cika mata kunne, yana ganinsa a hannuta sai yay shiru yana kallon Smart da sauke ajiyar zuciya. Zaune Smart ya kai kusa da Lulu cikin damuwa da ɗan murmushi, ya zubama yaron idanu da faɗin, “Kayi fushi da Papa ko Sweet heart? Kayi haƙuri Papa yayi laifi da baizo ya ganka ba tsahon lokaci. Please ka daina min ƙiwa kaji my sweet friend ɗina”. Ya ƙare maganar yana ɗan lakacema yaron hanci. Da sauri AA ya sake lafewa jikin Mamansa ya zata ɗaukar yasa zai sake yi.
Murmushi ya sake saki da girgiza kansa kaɗan. Sai kuma ya dubi Lulu dake saurarensu da kallo kawai. “Yana cin abinci ne?”.
Cikin ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki tana kallon yaron ta ce, “Da ga Kunu sai tea kawai yake sha, sai biscuits haka da ɗan sweets suma wani lokacin ko an bashi bai sha”.
“In dai ya biyo Babansa kam bazai sha ba, dan bana shan zaƙi nikam. Bari na haɗa masa tea ɗin maybe yunwa ce ta tashesa”. Kai kawai ta iya gyaɗa masa. Har ga ALLAH wannan halayyar tashi na saka mata ganin girmansa da kimarsa. A haka idan ka dubesa sai ka ɗaukesa a wani mutum mai jin kai da girman kai, amma sai ka zauna da shi kaga baida damuwa akwai sauƙin kai. Babu jimawa ya dawo da cup ɗin tea, zama yay a gabansu yana fuskantarsu, ya ɗan ɗebi tea ɗin a spoon ya kai bakin AA. A mamakinsu sai sukaga yaron ya ɗan kallesa kamar zai yi kuka sai kuma ya amsa. Dariya suka sanya su duka. Smart ɗin ya ɗan dungure masa kai da faɗin, “Ana son kayana amma ana guduna”. Ita dai Lulu dariya take musu. Tun yana amsa daga cinyarta harya zamo ya rarrafo jikinsa.
“Oh ashe ƙiwar bamai nisa bace Sweetheart”. Smart ɗin ya faɗa yana ɗaukarsa zuwa jikinsa. A haka ya cigaba da bashi tea ɗin suna hira da Lulu duk dai akan yaron ne da yanda yake samun soyayyar ƴan uwanta da nashi. Sosai Smart kejin ɗari a ransa, dan kuwa maganar nan ce dai ta malam bahaushe da kan ce mai ɗa wawa shima ke ɗawainiya da shi….
*_NIGERIA_*
A karo na farko tun bayan sakinsa da dawowarsa ƙasar yau sukai zaman meeting na farko da abokan cin mushen nasa. Wato Alh. Baita, Hon. Nakowa. Da Hon. Misau. Sai yaronsa Malami da aka dakatar daga waje kafin lokacin tasa shigowar yayi, dan akwai abinda ya ke son su fara tattaunawa da ba dole bane sai malamin yaji duk da kuwa a cikin sirrikansa babu abinda bai sani ba. Wani abu ma daya sani su su Alh. Baitan basu sani ba. Sun ƙara jajanta masa abinda ya faru cikin nuna ɓacin rai da tattara laifin gaba ɗaya akan Daddy da ɗan ka-ce-na-ce akan yanda akai suka san inda Lulu take. Shi dai shiru yay kawai yana saurarensu har suka gama bai ce uffan ba. Sai ma ya ɗakko musu batun kayan da yayo order da lokacin da yake ganin zasu iya shigowa Nigeria. Sun ɗan tattauna sosai akan hakan sannan suka dai sake komawa batun Daddy. Duk wani tsare-tsare a kansa sun yisa ne a wannan ranar harda ita Lulu da Smart suna a cikin plans nasu. Hatta da Abba wannan karon shima ya shigo lissafinsu…..
*_UK_*
…..Tunda suka dawo bedroom ɗin domin kwanciya sai tsoro ya shigi Lulu saboda ganin take-taken Smart ɗin a kanta. Sai dai tana ta ƙoƙarin basarwar cike da ƙarfin jali. Alwala tayo zatayi shafa’i da wutri yace ta jirashi. Jitai kamar zatai kuka, ta ɗan kai dubanta kan AA da ya haɗa da tarkacen kwalaben turarensa. Babu jimawa ya fito shima da alamar alwalar yayo. Kayan jikinsa ya canja zuwa jallabiya, cikin umarni ya jasu jam’in salla raka bibbiyu har sau uku, da ga ƙarshe suka rufe da shafa’i da wutrin. Juyowa yay gareta ya ɗaura hannunsa na dama saman kanta ya karanto addu’a. Zuwa yanzu tana da ɗan iliminta na addini gwargwadon iko, dan haka ta fahimci sallar da sukayi, duk da kuwa ita bawai ankawota bane matsayin amarya, sai dai a wancan lokacin ma ai sunyi irin sallar a randa komai ya shiga tsakaninsu. Sai ko ga shi shi da kansa yana faɗa mata cikin tsokana da murmushi ya ke cewa, “Kin san ke yau a amarya kike, dole ai miki tarba irinta amarya”.
Bata iya cewa da shi komai ba, sai dai tuni taji zuciyarta ta fara gudu a cikin ƙirjinta tuno da wahalar da tasha a waccan ranar da sakamakon abinda ya biyo baya na samuwar cikin AA. Sai ma taji ta gagara tashi a wajen. Ganin ya tashi shi ya koma saman gado waje ɗansa hankalinsa a kwance jiki a sanyaye ta jawo handbag ɗinta ta fiddo Alkur’ani itama ta fara karatu. Ta wutsiyar ido Smart ke kallonta yana jin wani irin farin ciki mara misali har tsigar jikinsa na tashi, sai dai baice komai ba dan a ganinsa lokacin cewar baiyi ba. Ya cigaba da yima AA wasa har yaron ya sake ɓingirewa barci. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali da kwashe kayan ya gyara masa kwanciya, dan tunda suka shigo Mamansa tai masa wanka da canja masa kayan barci, sai ƙamshi yake mai daɗi. Kwanciyar yay shirin yi shima abinsa bayan ya shiga bayi ya gama uzirinsa ya fito ya canja kayansa zuwa na barci da feshe jikinsa da turarruka ya haye gadon harda yin addu’ar barci. Hakan ya saka Lulu ɗan jin nutsuwa, ganin har ya ja bargo ya rufama kansa ta saki ajiyar zuciya. Mintuna kusan goma sha huɗu baya ta rufe Alkur’anin ta miƙe itama. A tunaninta Smart yayi barci. Toilet ta shiga ta ƙara gyara jikinta kamar yanda aka koyar da ita salo-salo a wannan fanin duk da ita batayi da manufa ba, dan bata ma fatan a kai ga hakan saboda tsoro yake ji sosai. Ta jima tana kallon kanta a mirror kafin tai ƙundunbalar fitowa. Ta ƙasan ido Smart da yay likimo yake kallonta, gaba ɗaya tsigar jikinsa ta shiga tashi dan rigar barcin da ke jikinta ba wata ta kirki bace, sai dai a gareta ita bawai tasa da wata manufa bane dan dama can tana sakawar a ita kaɗanta. Gadon ta nufa zuciyarta dai na kai-kawo, dan haka data ɗan kai zaune a bakin gadon ta tsurama Smart ɗin ido. Ganin bai ko motsa ba ta sake yarda yayi barci, sai kuma ta dubi a inda ya kwantar da AA, da ga gefensa sai dai ya kakkaresa da filos ta yanda ko juyi yay bazai faɗi ba, shi kuma ya kasance kamar a tsakkiyar gadon ya bar mata ɗayan gefen nashi. Sai da ta ɗan hararesa duk bata san yana kallonta ba sannan ta tura baki tana kaiwa kwance a hankali, tasan idan tace zata ɗakko AA ta maido tsakkiyasu Smart ɗin zai iya farkawa, koma yaron ya farka shi ya sanya mata daru duk da dai yanzu ya bar kukan dare, dan haka ta haƙura akan zuwa da safe dole a nema mafita, tunda dai taga ba ɗaki ɗaya bane a gidan ita zata koma wani ɗakin ta bar masa ɗakinsa, tun ma ɗazun da ace tasan nashi ne bazata yarda ta sauka anan ɗin ba. A hankali ta ɗan ɗaga bargon kaɗan ta yafama jikinta tana wani rumtse ido da cije lips, harda waigawa ta dubi Smart sai taga yana a yanda yake dai ko. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sake saki da lumshe ido ita a dole tasha da ƙyar.
Dariya Smart ke dannewa da ƙyar, sai da ya tabbatar ta gama dabarun nata sannan ya mirgino jikinta a hankali ya rungume ta tsam. A firgice ta juyo jikinta har yana rawa. Sai ya sakar mata murmushi da kashe mata ido ɗaya.
Muryarta har rawa take wajen faɗin, “Dama idonka biyu?”.
“A’a yanzu na farka” ya bata amsa cikin gimtse dariya.
Kallonsa take cikin rashin yarda da cewar yanzu ya farka wai. Zatayi magana ya ɗora yatsansa saman lips ɗinta da faɗin, “Shiiii!!!”.
Dole ta haɗiye maganar idanunta na kawo ruwan ƙwalla. Juyota yayi da ƙyau suna fuskantar juna, murya ƙasa-ƙasa yake magana yana busa mata iska a fuska. “Amarya mai tsoro da fa ƙyar take sha a hannun ango. Karki zama raguwa mana Nooru Nisa”.
Fuska ta ɗan ƙwaɓe kamar zata sakar masa kuka. Sai kuma cikin rawar murya ta ce, “Aliyu kaga dai ALLAH ni har yanzu wajen da akai min aikin nan bawai ya gama warkewa bane, sannan ma banda wani isashen lafiyar jik…..”
“Irin wannan sharhi haka Madam. Ni nace zanyi wani abu ne?”. Ya faɗa cikin katseta da kai yatsarsa saman lips ɗinta yana zagayawa. Sai kuma duk taji kunya ta lulluɓeta, irin wannan kama kai har ina. Shima murmushi yayi dan ya fahimci ya rufe bakin maganar, abin faɗar sun maƙale. Idanunta ta maida ta rufe a hankali tana haɗiyar zuciya, daga haka ta fara ƙirƙiroma kanta barcin dole. Jin numfashinsu ya sake kusanta da juna ya sata buɗe ido da sauri, sai dai kafin tayi wani yunƙuri lassafin ya canja, dan Smart ya rantse yau fa a angonsa yake, ya barta ne kawai ta gama kame-kamen nata……….✍️
Hummm🚴🚴🚴🚴
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣1️⃣
…….Al’amarin Umma kamar wasa ƙaramar magana ta fara zama babba. Dan ita kanta tun tana ɗaukar abun matsayin ba komai ba sai gata ta fara hawaye cikin tashin hankali. Dan kuwa dai ƙawarta Hajiya Naqiba tazo, amma tana shiga ɗakin nata itama da gudu ta dawo tana ihu mai firgitarwa da yafi na jama’ar gidan. Hankali tashe Umma ta biyota tana faɗin, “Na shiga Uku ni Yaha, Aminiya kema ɗin abinda suke min zaki min? Wai mina muku ne haka kuke irin wannan firgita da ni? Dan ALLAH ki faɗamin Aminiya kar ki min yanda suke min kema”.
Ina Hajiya Naqiba ba sauraren Umma take ba. Ihu kawai take kwarawa da iya ƙarfinta har maƙwafta da mutanen waje na iya ji, daga ƙarshe ma ta yanke jiki ta faɗi a sume dan Ummah taƙi daina binta. Cikin tashin hankali Umma ta isa gareta ta na jijjigata, a dai-dai nan mutane suka fara shigowa gidan da ga waje hankali a tashe. Ai sai ga maza na dafe huluna suna juyawa a guje. Duk wanda ya shigo yana tozali da Umma rungume da Hajiya Naqiba sai ya afa da gudu ya juya. Ba matan ba ba mazan ba ba yaran ba. Cikin ƙanƙanin lokaci zance ya zagaye anguwa. Masu ƙarfin hali na cigaba da shigowa domin tabbatar wa. Sai dai fa babu fashi duk wanda ya shigo zai juya a gujensa yana ihu da faɗin “Wayyo Dodo!! Wayyo dodo!!.”
Umma da ke zubama hajiya Naqiba ruwa tana kuka dan ganin abin da bana lafiya bane ta zabura jin aminiyar tata ta sake fasa gigitacciyar ƙara. Dan tana farfaɗowa taci karo da ita a kanta. Yin ƙurin da zatai domin ceton ranta ƙafa ta gurɗe jikake ɓass kamar an ɓalla katako ba ƙashi ba. Sai ta sake zubewa a ƙasa cikin wata irin wahalalliyar ƙarar azaba ta sake sumeya. Duk da abinda ke faruwa kaf ƴan gidan na maƙale ta windows suna kallo har ƴaƴanta da suka rarrabu. Wasu a ɗakin Ammah wasu na Mama. Ita dama aunty amarya da yaranta ɗakin Ammah suka afka suma. Ammah da al’amarin ya jijjiga ma zuciya na zaune a kujera tana cuɗawa da kwancewa. Dan in har lissafinta yayi dai-dai ƙaiƙayine ya koma kan masheƙiya fa a wannan karon. Tukunyar da suka gani tarwatse a tsakar ɗakin Ummah itace asirin da taima su Aliyu matarsa ke ganinsa da mummunan siffa irin wadda suke ganin Umma da ita a yanzun. Abba ne yay hikimar kiran yaranta na ma’auri da su Salim yace suzo babu lafiya. Dan shikam yama rasa ina zai kama a wannan lamari. A yau dai ya sake tabbatarwa Umma na bin bokayen tsubbu, kuma tabbas akwai ƙamshin gaskiya mai kamanceceniya da juna akan al’amarin Aliyu da matarsa da wanda Umma ke’a ciki yanzu. Yau matar Aliyu ta koma wajen mijinta, hakan na nufin komai ya daidaita tsakaninsu asirin ya dawo inda aka aikashi. Dama ai sharri ɗan aike ne, idan ya isar da saƙonka sai ya dawo ya tabbatar maka yaje. Har zai kira Smart sai kuma ya fasa cikin girgiza kai dan a yanzu ya tabbatar dare ne a UK.
Yaran nata ma koda suka iso duk wanda yay tozali da Umma sai gudun ceton rai. Umma ta fashe da kuka da tun ɗazun take irinsa har muryarta ta dishe. Ga aminiyarta kwance ƙafa sai kumbura take kowa ya kasa zuwa a taimaka mata saboda Umma da ke a wajen. Al’amarin dai sam babu daɗi, Umma na cikin tashin hankali fiye da wanda al’umma ke ciki akan ganinta a mummunar halittar da kowa ke ganinta. Ita kuma lafiya Lau take kallon kanta, dan har ɗaki ta nufa ganin kanta a madubi babu wata damuwa ko tawaya tattare da halittar ta sai fuskarta datai kace-kace da hawaye har idanunta sun kumbura. Kafin ta fito ne aka samu aka ɗauke Hajiya Naqiba dake kwance bata da banbanci da gawa. Dole asibiti aka wuce da ita a gaggauce dan ƙafar tayi masifar kumbura damm abin zattashin hankali……
*_UK_*
Wahala iya wahala Lulu tasha a wannan dare hannun Smart. Dan zata iya rantsewa ita kam bata ga banbancin sa da daren farkonsu ba, kodan ta saka ma ranta tsoron al’amarin ne oho. Amma tabbas ko a yarda da ita ko kar a yarda Smart namijin gaske ne da ko’a cikin mazan ma zai iya amsa sunan mazaje ne. Sai dai bata sani ba ko ragwantakarta yasa take masa irin wannan kallon ko kuma dan shi ta sani bata san sirrin sauran mazan ba.
Shi kansa sai da ya koma tausayinta, dan magana ta gaskiya fa bai raga mata ba, wahalarsa ta kusan shera ɗaya da wasu watanni sai da ya fanshe abinsa tsaff. Sai dai kuma shi a karan kansa bashi da zaɓin da ya wuce hakan. Bai sani ba ko tsananin begenta da yake a cikine ya sashi jin yau ɗin babu bambanci da wancan daren da ya kasa goguwa a zuciyarsa, amma ako ina kam zaiyi alfahari da baiwa irin ta matar tasa. Dan a wancan dare shima sabo yake, yau kam ya banbance tsakanin aya da tsakkuwa. Ya kuma zaɓi yimata mai gana ɗaya ne dan cire mata tsoron nan da ya lura yay mata tasiri. (Humm gyaran su iya Tabawa bai faɗi a banza ba kenan🥱🤣🚴).
Langyare iya langyare, raki iya raki yasha shi. Kuka kam muryarta har bata fita. Tun ana bashi haƙuri da roko da magiya har dai aka koma kiransa mugu. Yaƙushi da cizo duk ya samu rabonsa kafin duk wani ƙarfinta na neman ceton kai ya ƙare ta koma zallar hawaye da jiran mala’ikan mutuwa (acewarta🥱😜😂).
Shi ya fara farkawa lokacin da alerm ɗin da ke tadashi sallar asuba ya kaɗa. Da ƙyar ya iya buɗe idanunsa da ke jingim da barci dan basu wani jima da kwanciyar ba. Hannu ya kai ya kashe alerm ɗin gudun kar AA ya tashi shima. Tunda ALLAH ya taimakesa dai har ya gama bidirinsa na daren jiyan yaron bai farka ba. Idannunsa ya zubama fuskar Lulu dake barci kamar a wahale, shi sai ma ta bashi dariya, dan haka ya ɗan murmusa da kai hannu ya shafa fuskar tata. Baki fal tsiwa da rashin ragiya amma sai tosoro da ragwantaka uwa farar kura. Ɗumin da yaji a fuskarta ya sashi jan bargon kaɗan yasa hannunsa a wunyanta. Zazzaɓine sosai a jikin nata kam kamar yanda yaji. Idanunsa ya ɗan lumshe ya buɗe da sumbatar goshinta yana sake matseta a jikin nasa cike da tausayawa.
“I’m so sorry Final Choice. Aliyu bazai sake baki wahala ba da ga yau kinji”. Ya sake kai mata sumba a saman hanci yana mai sake jinta sama can ƙololuwa a zuciyarsa. Da ƙyar ya iya samu ta tashi sai faman langyare take masa da kukan shagwaɓa. Shi dai biye mata yake yana binta da lallashi. Dan ko a wancan karo na farko ba’ai masa wannan langwai ɗin ba. Koda yake wancan ana bori yaushe ma ya samu kanta. Dan haka yau kam ya ƙudiri aniyar rama mata dukkan tattalin da bata bashi damar yimata a waccan ranar ba. Yanzun ma taimaka mata yay ta sake ɗan gaggasa jikinta, duk da dai yasan taimakon da yay mata jiya kawai ya wadatar, yasan kam harda raki da ragwantaka dai koma yace shagwaɓa. Shine ya jasu salla yanzu ma, suna idarwa ya miƙe ya fita, bai jima ba ya dawo ɗauke da kofin tea da soyayyen ƙwai. Da ƙyar ya samu ta sha tea ɗin, kwan ko bata ko kallesa ba balle ta ci, sai maidashi yayi. box ɗin magungunan sa ya ɗauko ya bata na zazzaɓi tasha da rage raɗaɗi. Sai da ya ga ta sake komawa barci ya sauke ajiyar zuciya. Yasan koyaushe AA zai iya tashi shima, dan haka ya haƙura da fita ko’ina motsa jiki ya ɗan yi a gida. Ilai ko bai jima da farawar ba AA ya farka. Rarrafawa yay kan Lulu yana kuka. Hakan ya sakata farkawa. Harararsa tayi, itama kamar zata saki kukan ta ce, “Ni bazaku kasheni ba kai da ubanka wlhy. Kai tayi idan ya jika yazo ku ƙarata”.
Kaf a kunnen Smart dake shigowa, dan haka ya saki murmushi yana ƙarasowa ciki. Tana jin motsinsa ta maida idonta ta rufe kamar barci take. Nanma murmushi yayi kawai da ɗaukar AA dake neman yimasa ƙiwa kamar jiya. Tsaff yama yaron wanka duk da dai da ƙyar akasha, dan sau kusan biyu yana neman suɓuce masa ALLAH dai ya kiyaye baisha ƙasa ba. Ganin kamar yunwa yaron keji yay zaman fara bashi tea da dama ya haɗo ya ajiye tun ɗazun kafin ya shiryashi yana nishi da ƙyar dan bai iyaba. Pampa’s ma da ƙyar aka iya sawa sai da ya duba a net.. yaga yanda akeyi. Duk kuma abinda sukeyi Lulu na kallonsu dariya kamar ta kasheta amma ta zaɓi yin likimo wai ya ɗanɗana yaji shima idan da daɗi. Shiko a zatonsa barci takeyi, sai da ta kasa riƙe dariyarta dai tayi sannan ya farga idanunta biyu. Cikin kalar tausayi yake kallonta da faɗin, “Yanzu nan idonki biyu aketa wannan dambarwar amma babu ko taimako Baby luv?”.
“Ku ƙarata nima ta kaina nake”. Ta faɗa tana masa gwalo da jan bargo ta rufe har kanta. “Haka kikace ko? Ba komai zamu rama ne ai”. Bata sake magana ba tai luf a bargo abinta tana dariya har suka kammala ya hawo gadon da yaron yana sauke numfashi ɗaɗɗaya. Sauka da ga jikinsa AA yay zai haye kan Lulu ya riƙoshi yana faɗin, “A’a Sweet heart abar Momy ta huta kaga Papa ya koya mata karatu duk ta jikata”.
“Yaushe ka koyamin karatun?”. Lulu da bata fahimci inda ya dosa ba ta faɗa tana buɗe kanta da sauri harara idonta kamar zai faɗo. Gira ya ɗaga mata da kashe ido ɗaya ya ce, “Yanzu ma malamin a shirye yake in har za’a barsa ya ƙara ɗora sabon darasi”. Yanzu ne ta farga da inda zancensa yaya dosa. Bargon taja ta sake rufe kanta da faɗin, “ALLAH dai ya shiryeka Aliyu. Ni kutashi ku fita barci nake son yi kun daman”.
“Amin ya rabbi tunda addu’a aka min. Amma fa babu inda zamuje muna nan tare da ke”.
“To ku koma ƙasan carpet kun ishan ALLAH”.
“Anƙi ɗin”.
Harararsa tai shi da ɗan nasa ta matsa can ƙarshen gado ta sake jan bargo dan da gaske jikinta ciwo yake mata sosai, ga zazzaɓi. Murmushi yayi da binta da kallo, dan yasan da gaske bata da lafiyar, yana mata hakane danta saki jikinta dai ne kawai. Wasa ya cigaba da yima AA dake son shi kawai a saukesa yayi ɓarna, sai da ya tabbatar tayi barci ya ɗan janye mata bargon da ga kan fuska danta samu iska. Goshinta ya taɓa yaji da ɗan sauƙin zafin, sai kuma ya maida kan wuyanta. Shima dai alhmdllh ya fara sauka. Sai ya samu kansa da sauke ajiyar zuciya……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣2️⃣
_______________
……..Kuka take sosai a gaban mijin nata da ayanzu al’amuransa ke bata tsoro matuƙa. Gaba ɗaya ya sauya mata, sauyawa irin wadda bata taɓa zato ko tsammani ba. Kai koda a mafarki ko lissafin rayuwa bata taɓa tunanin itada Sufiyanun nata zasu kasance a irin wannan ajin ba. Amma a yau sai gashi wai harda mata kishiya sa’ar jikokinta da wannan shekarun nata tsofai-tsofai. Kuma ko kunyarta baya ji yake soyayyarsa kamar wani ƙaramin yaro.
Baba Garko da tunda ta shigo ta zauna bai ko ɗaga kai ya dubeta ba sai ma wayoyinsa da yake hankali kwance. Daya gama wannan zakaga wata ta shigo. Cikin jin gundura da kukan da take rera masa ya ce, “Amma dai kin san kina damuna ko? Please bana son damuwa idan kukanki zakiyi zaki iya bani waje”.
Sake ɓarkewa tai da sabon kuka kamar wata ƙaramar yarinya. A dai-dai nan akai knocking ƙofar falon, ɗan jimmm yay yana kallon ƙofar kafin ya ce, “Ko waye ya shigo”. Mai aikin amaryarsa ce ta shigo a rikice, amma hakan bai hanata kaiwa tsugunne da ga bakin ƙofa ba ta gaisheshi cikin girmamawa sannan ta ɗora da faɗin, “Alhaji aunty amarya ce bata da lafiya, tun ɗazun kuma ta hana azo a sanar mak…” ai mai aikin ma bata ƙarasa rufe baki ba ya miƙe zaram ko nauyin tsufarsa baya ji. Ƙofar ya nufa a hanzarce, Dada da kanta ya nema tarwatsewa ta bisa da kallo galala, wani irin tuƙuƙin baƙin ciki na sake turniƙe mata zuciya. Ba’a ko rufa minti huɗu ba sai gashi ya shigo a rikice, ko kallon inda take baiyi ba ya shige bedroom ɗinsa. Cikin ƴan sakanni ya sake fitowa ya fice hannunsa riƙe da key ɗin mota ya canja zuwa jallabiya. Kasa motsawa tayi a wajen har sai da taji ƴar hayaniya na tashi ta miƙe jikinta na rawar ɓacin rai ta leƙa ta window. Akan Baba garko da ke rungume da amaryarsa ita kuma tana faman yarfe hannu tana kuka idanunta suka fara sauka. A take zuciyarta ta ayyana mata haihuwa. Sake dugunzuma zuciyarta tayi har tana jin jiri na neman kwasarta, batama san sanda ta sulale a wajen ba ta zube saman kujera jaɓar wasu zafafan hawaye na wanke mata fuska, sai kuma ta ɓarke da kuka. Tunda take a rayuwarta, bata taɓa shiga matsanancin baƙin ciki da tashin hankali irin na wannan gaɓar ba. A tsahon rayuwar ƙuruciyarta ko firar kishiya bata so, kai ko ƙawa ko cikin ƴan uwa akaima wata kishiya daina zuwa gidan mutum take saboda yanda ta tsani kishiya. Amma a yau sai gata da ita a wannan shekarun nata, harma da ciki na haihuwa…..
(🤣🤣🤣🤣🤣 Kar kuce dariyar mugunta nakema Dadaras😜)
____________★
Tun Ummah na ɗaukar al’amarin ta ƙarami harta fahimci ya wuce da saninta. Kuka ma da hawaye yanzu ta kasa yinsa. Ƴan gidansu sunzo sai dai me suma ƙarewa sukai da fita da gudu harda masu faɗuwa. Wajen Abba suka koma kowa na maida numfashi, yayanta cikin damuwa ya ce, “Anya ba aljanune suka shigi Yahanasu ba Yaya Mika’il”.
Cikin ɗan taɓe baki Abba yace, “Idan ma sune wajen biɗar baƙar tambayarta ta kwaso su. Ballema bana jin hakanne. Nafi ƙyautata zaton ƙaiƙayine ya koma kan masheƙiya. Ni yanzu jibirin ban san yanda zanyi da wannan matar ba. Gaba ɗaya ta firgitamin iyali sun kasa sakewa kowa sai zaman ɗaki”.
Cikin damuwa Jibirin yace, “Amma yaya bai kamata kace haka ba. Ƙilama cikin matanka wata taimata haka kasan dai mata akan kishi”.
“Wane matan nawa? A’a ƙarya haramun. Ai duk cikin iyalina babu fanɗararre irin Yaha. Nasan halin kowacce a cikinsu da abinda zata iya. Na jima ina zarginta dama da shigen-shigen nan kawai dai ban taɓa gani da idona bane shiyyasa ban kafa hujja ba. Amma a yanzu na gama fahimtar komai. Ko wannan halin da kaga tana cikin sihirin da taima Aliyu da matarsa ne ya dawo mata…”
“Aliyu kuma Yaya? Aliyu Aliyu dai namu na nan?”.
“Shi ɗin fa”.
“Ikon ALLAH! To shi Aliyu dake matsayin ɗanta kuma zatama asiri. Miye ribarta kenan?”.
“Oho mata, ita ta sani”.
Sosai al’amarin ya girmi kan kowa. Cikin ƙarfin hali Zaidu ya bada shawaran to ko za’a samo malamai suyi addu’a ne. Dan wannan yanayin nata abin tashin hankali ne ga kowa tunda gashi hankalin kowa a tashe, shi wlhy yanzu haka baya jin yau ɗin nan zai iya barci lafiya saboda ganin wannan mummunar halitta da Ummah ta koma. Abba dai yace shi babu ko sisinsa a nema mata lafiya. Hasalima ya kirasu ne su wuce da ita dan bazai iya ba. Hankalinsu ya tashi matuƙa, dan sukam bazasu jajibi wannan halittar ba sukai cikin iyalinsu suna zaune ƙalau. Dan haka suka dage bashi haƙuri da roƙo da magiyar ya barta a ɗakinta cikin ƴaƴanta harta samu lafiya sai aji dalilinta na wannan mummunan al’amari, idan ma matakin sai ɗauka sai ya ɗauka. Anfi ƙarfin Abba ne kawai, dan haka yay shiru. Su suka fita suka zo da malamai, da ga tsakar gida suka tsaya aka kwala mata kira ta fito. Su kansu malaman sai da suka zabura da ganin mummunar halittar dake tunkarasu, ganin tana yo kansu gadan-gadan sukaji fa dauriya ba tasu bace. Ai tuni suka dafe kawuna kowa ya ara cikin ta kare yana jan kula’uzai. Bayan su an sake kawo wasu malaman amma fa kowa yazo yana tozali da Umma sai dai a tsincesa waje ya dafe ƙeya. Al’amari kamar wasa sai ƙara faɗi yake. Dan takai ƴan jarida daga gidajen rediyo har sun fara zuwa neman labari. Sai dai suma fa suna shigowa sukai ido huɗu da Umma labarin bai ɗaukuwa garesu sai ƴar reren gudu…
Tsabar tashin hankali da hawan jini Umma ta koma ko gani batayi da ƙyau. Barci kuwa ya ƙauracema idanunta gaba ɗaya. Cikin ƙanƙanin lokaci tai wata irin muguwar rama mai ban tsoro. Babu abinda ke ɗaga mata hankali sai ganin ƴaƴanta suma gudunta suke da mijinta da ta ɓata tsahon shekarun rayuwarta tana faɗa da faɗi tashi a kansa. tana son jin halin da Hajiya Naqiba take amma babu hali. Rayuwa ta mata duhu, duhu irin wanda ko tafin hannunka baka iya gani, duhu irin wanda zuciya kanta bata iya tuna komai sai ƙunci da ciwo mai raɗaɗi. Hatta salla yinta kawai take amma bata ma sanin mitake yi a cikinta. wanka kam bama’a maganarsa dan tashin hankali. abinci dama yanzu ƙofar ɗaki Abba ke zuwa ya ajiye mata saboda kowa tsoro yake ji, shi kansa dai tausayin rai ne ke sakashi yin ƙarfin halin ajiyewar kawai dan an hanata fitowa…..
*_★UK★_*
Sosai tasha barci, dan ko da lokacin salla yayi da ƙyar ya iya tashinta tayi ta sake komawa. Bata tashi ba sai gab da la’asar. Yana falo suna kicimilli da ɗansa ta fito. Tsaye kawai tai tana kallonsu har bata san tana murmushi ba. Mayataccen ƙamshinta ya fargar da Smart kasancewarta a wajen. Zaune ya tashi da ga kwancen da yake yana ɗaga AA dake sukuwa a saman cikinsa. Cikin lumshe ido da sakar mata murmushi ya ce, “Kin tashi?”. Cikin falon ta ƙarasa takowa tana marairaice fuska. Hannunsa ya miƙa mata alamar tazo garesa. Babu musu ta ƙaraso, ya riƙo hannunta ya zaunar gefensa yana mai rungumota ta gefen jikinsa kanta a saman kafaɗarsa. AA dake neman haye mata jiki ta dungurema kai batare da tayi magana ba. Smart dake kallonsu da murmushi ya shafo fuskarta da faɗin, “Yaya jikin naki?”.
“Ba sauƙi”.
Ta bashi amsa cikin tura baki.
Sosai ya waro idanunsa waje. “Ba sauƙi fa Nooru Nisa”.
Fuska a gimtse ta ce, “Eh mana dan ni dai jikina ciwo yake mun har yanzu”.
“Kai Madam bansan ragwantaka fa. Ni da nake shirin yanzu a sake tafiya yaƙin ƙasa da ƙasar again.”
“Dawa?!”.
Yanda tace dawa ɗin cikin waro idanu da ƙwaɓe fuska kamar zatayi kuka ya sashi kwashewa da dariya. Mintsini mai zafi ta sakar masa tana miƙewa. Ya riƙe wajen da sauri yana yamutse fuska da faɗin, “Wai ALLAH na! wannan zalincin fa? Kefa kin iya mugunta”.
Gwalo ta masa tana dariya, ta ce, “Mugayen ai da yawa kai ne malamina”. Tai wucewarta kitchen Dan yunwa takeji.
“Haka kika ce ko? Ba komai zan rama ne”.
Dariya ta shige tanayi, babu jimawa ta fito ɗauke da apples data yayyanka a ƙaramin bowl. Ƙasa ta zauna dan taji daɗin miƙe ƙafa. Smart dake binta da kallo ya ce, “Badai wannan ne abincin ba?”.
Muryarta a marairaice da shagwaɓa ta ce, “ALLAH bakina babu daɗi, ina son naci kozai washe. Sannan wannan ɗin ma ni kam ya isheni”.
Idanu kawai ya tsira mata yana kallonta. Ta ɗan hararesa da faɗin, “Kallon fa?”. Murmushi yayi da janye idanun nasa cikin yin luuu da su. Sai kuma ya sake zuba mata su cikin yanayin kasala. “Yarinyar nan anya kuwa?”.
“Anya kuwa mi?”.
“A’a ni bance komai ba. Kawai dai dama sai nake ga kamar fa wannan karon ma kin amshe ne, kin san fa ni bana saɓa saiti a zahirin fili wasa da na ɓoye”.
Da farko bata fahimci mi yake nufi ba. Sai da tai ɗan shiru sai kuma ta dago ta hararesa. Dariya ya ƙyalƙyale da shi, zai sake magana ta tura masa Apple ɗin data tsiro a bakin tana sake harararsa. “Kai dai ALLAH ya shiryeka wlhy”.
Murmushinsa ya cigaba da yi shi dai, koda ya shanye apple ɗin data saka masan sai ya sake matsowa da buɗe baki wai ta ƙara masa. Kafaɗa ta maƙe alamar anƙi ɗin. Ya bata fuska cikin yanayin shagwaɓa. “Kina sha, kina bama AA ni kuma sai a wareni. ALLAH sarki nima da Ammah na kusa da banga haka ba. Bari na kirata na faɗa mata”.
Da sauri ta fisge wayar ta tura ƙasan ƙafafunta. Sannan ta tsiro apple ɗin ta tura masa abaki tana harararsa. “Mai kwaɗayi, kai yanzu in an barka saika faɗa?”.
“Sosai kuwa. Harma da Daddy da Abba duk zan kira, ince tunda kika zo baƙya kula da ni.”
“Sharri Master kenan. Daka kasheni dan ina jin kunyar Abba sosai ALLAH.”
“Ni kuma baƙya jin kunyata ko?”.
Murmushi tayi tana sakama AA da ke tsaye jikinta yana wasa da gashinta apple ɗin a baki. Cikin basar da zancensa ta ce, “Da kai Daddy ya haɗa baki kuka kawoni nan ko?”.
Kwance ya kai yana ɗora kansa a saman cinyarta, sai da yay ƴar dariya da tsokano AA ya ce, “Nikam babu ruwana. Daddy ne yay miki wayonsu na manya saboda yana jin tausayina. Shekaranjiya dai muna magana da shi yake cemin akwai saƙo da zai aiko min da shi, idan kuma ya samu shigowa London to, dan zaije Manchester city ne”.
“Lallai ma Daddy nice saƙon yake nufi ko mi! Sai kace wata kayan wanki”.
Dariya sosai Smart ke ƙyalƙyalawa har AA na faɗawa jikinsa shima yana tayashi. Sai kawai Lulu ta zuba musu ido tana kallo. Sai da sukai mai isarsu ya jiyo yana kallonta. Ganin yanda ta zuba musu ido ya ɗan ɗage gira da faɗin, “Kallon fa Madam”.
“To ba dole na kalleku ba naga kun zare. Wai nikam dama kana dariya har haka? Amma da kaita tsuke fuska kamar wanda akaima saƙon mutuwa!”.
Kansa kawai ya shafa yana murmushi baice mata komai ba. Itama sai ta share ta cigaba da shan Apple ɗin ta. Lokacin-lokaci tana saka masa a baki shi da AA da ke saman jikinsa yana wasa da ƙasumbarsa…….✍️
_🚴Ya kamata mu taya Ummah da Addu’a 🥱🥱🥱_
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣3️⃣
…….Haka suka cigaba da kasancewa cikin farin ciki da nishaɗi a wannan yini. Sai zuwa wani lokaci yayi kiran Ammah kasancewar su a Nigeria ba daren bane. Sun gaisa sai yake jinta kamar cikin damuwa. Cikin kulawa ya shiga jera mata tambaya. Sai cewa tai babu komai ya haɗata da Mawaddat. Kafin ya bama Lulun ne take tambayarsa babu dai wata damuwa kowa?. Ya ce Alhmdllh yanzu haka ma gasu nan AA ya ishesa da ɓarna. Murmushi Ammah tayi har yana iya jiyo sautinsa. Ta ce, “Ai wannan baban nawa yana ji da ƙarfi da lafiya ne, nima ɗakina ya huta da ɓarnarsa ai yanzu, ga shi nan duk yamun fashe-fashe kala da iri. Dan Babana ne kawai yasa bance a biyani ba”.
Cikin dariya Smart ya ce, “Ai ba’a shiga tsakaninku da Baban naki kam Ammah. Sai dai nayi mamakin yanda yay girma haka, ashe hoto na rage min girman nasa.”
“Ai duk kai ya kwaso Hydar. Babu wani abu naka da yaron nan ya bari. Yanzu dai Alhmdllh komai ya zama labari, sai ku sake dagewa da addu’oi dan ita matsalar rayuwa da jarabawa basa ƙarewa. Idan wannan ta wuce watace kuma zata iya kutso kai a kowane irin lokaci. Abinda dai kawai ake buƙata shine bawa ya tsarkake zuciyarsa kada ya nufi kowa da sharri, domin shi ɗan aike ne duk inda ka aikashi sai ya je ya dawo ya tabbatar maka yaje. A zauna da mutane lafiya dan ALLAH, kar a zalunci wani koda da ganganci ne, idan kaima mutum kuskure ka bashi haƙuri ka kuma nema afuwa, sannan ka gyara wannan kuskuren. Ga matarka nan dai ta dawo gareka, sai aji tsoron ALLAH ka sauke hakkokinta da ALLAH ya ɗaura maka, karka zalunceta saboda kana amsa suna Namiji shugaba ita tana mace kai rauni, karka ce akoda yaushe dole kaine a sama da ita, shi aure ƙauna da haƙuri da kawaici ke jagorantarsa yay ƙarko. Sannan shi babba shi aka sani da shanye komai daga na kasa da shi, idan laifi tai maka kayi nazari da bincike kafin yanke hukunci, karka yarda ka yanke hukunci cikin fushi, karka yarda kace zaka zagi iyayyenta a bisa kuskurenta, kada ka aibantata ko hantararta dan kawai ta maka abinda bashi kake so ba. Nasiha da jawowa a jiki shike saka zuciyar waninka maka biyayya komai taurinta, a duk lokacin da ka kasance mai adalci da tattalin rayuwar mace da ƙyautata ma da yin haƙuri da ita ba sai kace ta kiyayeka ba, ita da kanta zata dinga jin shakkar maka laifi ma, bakuma zata taba samun nutsuwa ba idan ta ganka cikin damuwa. A duk kuma sanda tai kuskure ka tsawata mata zata fahimceka fiye da yanda kake buƙata. Ka yabama matarka a duk sanda tai abu mai ƙyau, ko kwalliya ta maka kwarzantata ka nuna mata duk duniya babu ƙyaƙyƙyawa a wajenka sama da ita, idan girki ta maka nuna mata tafi kowa iyawa, babu kuma wani abinci dake maka da ɗi sama da nata. Idan tana magana da kai ka bata hankalinka da ɗaukar kowane furucinta da muhimmanci koda kai a wajenka bamai muhimmanci bane. Ina mai tabbatar maka Aliyu matarka saita maidaka tamkar sarki, zaka zama ɗan lelenta, zaka zama amininta, zaka zama mata ɗan uwa, zaka zamar mata jarumi, zataji babu wanda take so ta birge a duniya sama da kai. Komai iyawar waninka za taga taka itace a sama da kowa. ALLAH ya baku zaman lafiya da zuri’a mai albarka. ALLAH ya kiyaye gaba”
“Amin ya rabbi Ammah, in sha ALLAHU zaki sameni mai biyayya akan shawaranki da umarninki. Nagode sosai, ALLAH ya ƙara muku lafiya da tsohon rai mai albarka. Ga Mawaddat ɗin dan naga ta ƙagara kamar ta kwace wayar”. Dariya Ammah tayi, yayinda shi kuma yake mannama Lulu wayar a kunne yana dungure mata kai. Alamar zan rama tai masa tana faɗin, “Ammah na” cikin zumuɗi. Cike da farin ciki itama Ammah da ga can ta amsa mata da “Na’am Mawaddat ɗina. Kun sauka lafiya ko?”.
“Lafiya lau Ammah ina yini?”.
Da kulawa Ammah ta amsa mata da tambayarta AA. Tai murmushi kawai batace komai ba dan sosai take jin nauyin Ammah akan al’amarin AA ɗin. Ta rasa miyasa hakan. Saboda ita kaɗai take iyama wannan karan. Garama Mommy itama akan ɗan ɗaga mata ƙafa wasu lokutan. Hira sukayi da Ammah sosai, itama tai mata nasiha tamkar yanda taima Smart, dan tana jinta babu bambanci da ƴaƴanta ne, sosai Lulu taji daɗin shawarwarin Ammah, harda ƴar ƙwallarta. Sun cigaba da hira har takai kunnen Lulu ya jiyo ihu da hayaniya. A tsorace take cema Ammah suwa ke ihu haka?. Rasama mi Ammah zatace mata tayi, shima Smart jin an ambaci ihu ya amshi wayar yasa a hansfree. Cikin ƙarfin hali Ammah ta ce, “Babu komai yara ne ke wasa”.
Haka kawai Smart yaji bai gamsu ba. Amma sai baice komai ba har sukai sallama. A yanayin damuwa Lulu ta ce, “ALLAH kamar Ammah na cikin damuwa”.
Kai Smart ya jin jina mata. “Tabbas akwai abinda take ɓoyewa. Kuma tunda kikaga taƙi faɗa mana bamai daɗi bane. Ina zuwa bari na kira Aunty Bilkisu”.
Wayar ta miƙa masa, yana kira kuwa aka ɗaga. Bayan sun gaisa ya tambayeta yaya jikin ta. Ta amsa masa cewar da sauƙi. Sai dai jiya mai gidanta yayi maganar cewar wai zai kaita Egypt, “Amma ina zargin dan Abba yay masa maganar cewar kace zanzo wajenka naga likita ne. Dan tunda matarsa ta dawo na kasa gane kansa a gidan nan Aliyu. Ni wlhy zaman nan yama isheni. Hatta yaran nan baya shiga harkarsu, jiya dan Sadiq yay faɗa da yarinyar wajenta bakaga dukan da babban yaronta yay masa ba, wai nayi magana shine yake faɗin banda haƙuri akan yara da kawaici.”
Sosai ran Smart ya ɓaci, amma sai ya shanye cikin danne zuciyarsa ya shiga bata haƙuri da lallashinta akan karta damu. A yanzu haka ma yana nan yana mata shirin tahowar cikin satin nan Ahmad zai zo ya kaita tayi visa, shi kuma mijin nata ta share batunsa kawai. Yaran kuma ta kaisu wajen Ammah daga can a dinga kaisu makaranta. Taji daɗin shawararsa sosai. Da ga haka take tambayarsa ina Mawaddat. Shekaranjiya abinda ke faruwa a gidan nasu yasata ɗan taƙarƙarawa taje shine Ammah kece mata ai sun komo wajensa. Har take tsogumin basuje musu sallama ba shine Ammah tace ai tafiyar ta shamattace akai babu wanda ya sani..
“Wani abu ya faru a gidan ne?”.
“Ammah bata faɗa maka bane? Ai mugun abin waccan azzalumar matar data muku ne ya koma kanta. Dan yanzu bakaga yanda ta koma wata irin mummunar halitta ba wlhy Hydar. Kowa fa bai iya zuwa inda take yanzu gidan nan cika yake da ƴan kallo harda ƴan jarida. Ai Umma taga ƙarshenta”.
“Ni duk kin sake dilmiyar dani wlhy Aunty. Please kimin dalla-dalla miya faru da Ummahn?”.
Tsaff aunty Bilkisu ta zayyane masa labarin abinda ya faru tun jiya da Lulu ta taho. Sosai suka girgiza da jin wai Ummah ce ta musu asirin nan, kuma yanzu haka ma kowa ita yake zargi akan abinda ya dinga faruwa da shi lokacin da yake faɗuwa idan ya shiga filin ball. Komai bai iya cewa ba sai ALLAH ya ƙyauta ganin yanda Lulu duk ta ruɗe harda su kuka. Dole yay sallama da aunty Bilkisu ya rungume matarsa a jikinsa yana sauke ajiyar zuciya. Gaba ɗaya idanunsa sun kaɗa sunyi jazur. Ganin yanda Lulun ta tsorata ya sashi ɗan sakin jikinsa shi. Fuskarta dake cikin tafukan hannunsa ya ɗago suna kallon juna. Ya ɗan ɗaga mata gira cike da tsokana. Sai kawai ta sake fashe masa da kuka. Dariya yayi a karo na farko. “Wai anya kuwa keda AA kunada maraba kuwa?. Shagwaɓanki yayi yawa. Yanzu minene abin kuka anan?. Ko kina jin haushin an rabaki da mijinki ne harna wata kusan goma bakiji ɗuminsa ba. To yanzu ba gaki tare da ni ba barci sai inda kika zaɓi kwanciya a jikina”.
Hararsa tai tana ture masa hannu. Shi kuma ya cigaba da dariyarsa yana kai mata kiss a fuskar. Bai barta ba sai da ya ga ta saki jikinta har tana dariya. Cikin sakin ajiyar zuciya a jajjere ta ce, “ALLAH naji tsiro ne Aliyu. Ni dama matar nan haka kawai bana sonta. Ashe muguwa ce. Kenan fa tana cikin wani ƙungiyan secret ne?”.
“Secret kuma?”.
“Eh mana tunda gashi tana iya turama mutane Dodo”.
Fuskarsa da murmushi ya ce, “Ba wani ƙungiya. Kin san a ƙasar hausa mata sun ɗauki kishi wani babban al’amari. Wasun ku zasu iya aikata komai saboda wannan kishin nasu. Bansan dalilin Ummah na aikata min hakan ba, dan ni taimawa ai. Amma nasan koma minene yana da alaƙa da kishi. Na jima da fahimtar ta tsani Ammah da mu kammu. Dan lokacin da akace na aureki baki ji yanda ta tada hankalinta wai na auri ƴar gidan masu kuɗi. Hakama aurarrakin su Hawwah”.
Cikin mamaki Lulu ta ce, “Oh dan gidanmu da kuɗi ka auran shine matsala kuma?”.
“Su haka suke gani. A tunaninsu ƴar masu kuɗi sai ɗan mai kuɗi. Idan ma za’ai irin wannan auren bisa ƙaddara ɗan mai kuɗi ya auri ƴar talaka yafi ƙayatarwa suke gani. Amma idan ƴar mai kuɗi ta auri talaka kamar zai zama ƙarƙashin mulkin mallakarta ne. Koda yake mafi yawa hakan ce ke faruwa shiyyasa tunanin duk mutanenmu yake a iri ɗaya.”
Baki Lulu ta taɓe kawai. Kamar bazatace komai ba sai kuma can tace, “Ni wannan abin ban ɗaukesa wani abu ba. Kowa bada yanda ALLAH ke son ganinsa ba. Talakawa nawa ne keyin arziki, masu ƙuɗi nawa kuɗinsu ke ƙarewa su koma abin tausayi. ALLAH da Daddy na bani tarihinsu shi da su Mommy da Uncle You har kuka nayi, kaga suma da basu da komai, amma yanzu fa. Kuɗin da duk mutuwa kowa zaiyi ya barsu ma”.
Kallonta Smart yake cike da jin ƙaunarta, bai taɓa sake tabbatar da tanada hankali ba sai yau. A hankali ya jawota jikinsa ya rungume tare da kai mata kisses tako ina a jikinta. Batai yunƙurin ƙwace jikinta ba kamar yanda ta saba. Sai da taga yana neman sakin layi ne ta shiga turesa, sai dai shi ya riga ya kai inda baya jin kira, dan haka ya ɗakko sabon salon kashe mata jiki har ya ɗauki hanyar cimma burinsa. Sosai ta rikice masa dan a tsorace take da al’amarinsa. Shi kuma ya tabbatar mata da babu gudu babu ja da baya. Duk da yau bata sha wahalar waɗan can matakan ba yanzun ma dai taji a jikinta. Shi kuma yasha raki da langaɓe. Lallashi yay tayi shi dai kam tunda ya samu yanda yake so. Bai kuma wani ja dogon lokaci ba ya sake nuna muradinsa, sai ta sanya masa kuka harda cewa ita Nigeria zata koma bazata iya da shi ba gaskiya. Dariya yayta dannewa, bai kuma ƙyaletan ba sai da ya samu yanda yake so. Aiko yasha baƙar magana a wannan yini, harda cewa sai ta gaya shi da Uncle Yousuf da Ammah. Ya ko miƙo mata waya cikin gyatse ya ce ta kira. Amsa tayi zata kira ɗin kuwa. Yanzu ya sake tabbatar da wautar ɗiyan madara, dan sai fisge wayar yay ya ɓige da cema Uncle Yousuf ya kira ne su gaisa. Dariya Lulu ta koma yimasa harda gwalo, dan ita wasa take masa, yo hauka take tacema Uncle Yousuf ɗin mi ma. Ta kula kallon yarinya Smart yake mata, shiyyasa take zuba masa taɓarar yaran aje a hakan……..✍️
_Kiyi son ranki Dan lokacinki ne ta wajen mu🥱😂😂🚴🚴_
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣4️⃣
…….Smart ya samu zama da Daddy da ya shigo London a ranar da Lulu ke cika kwanaki biyar. A ranar sun buga wasa a cikin London ɗin ne, bayan sun tashi ne sukai zaman tattaunawa su uku harda Uncle Yousuf da ya shigo domin kallon wasan shima. Daddy ya damƙa masa camara, tare da tabbatar masa Sulaiman yana shiri na musamman a kansu. Dan a yanzu haka akwai wata yarinyar baturiya da ya gano an turota ta shiga jikin Smart ɗin. Shiyyasa ma yay azamar kawo masa matarsa kusa da shi saboda gudun kar’a samu akasi. Murmushi Smart yayi da firzar da iska. Kansa a ƙasa ya ce, “Karka damu Daddy in sha ALLAH babu abinda zai faru. Kafin na mallaki iyali nafi ƙarfin kaina ma balle yanzu da na tabbatar da har zuri’a na fara tarawa. In dai al’amarin Sulaiman ne yabar damunka, dan a yanzu haka a tafin hannunmu yake. Abinda nake buƙata a wajenka kawai yanzu bayan wannan camara ɗin shine list ɗin abokan huɗɗarsa. Sannan ka sa su Hassan subar Abuja su koma Kano gabanku. Dan Sulaiman ya fara kai musu hari ta hanyar aboki, a yanzu haka ana gab da jan ra’ayinsu da wani kasuwancin da nake ƙyautata zaton irin shigo-shigon da akai maka ne”.
Sosai hankalin Uncle Yousuf da Daddy ya tashi, dan sam Daddy hankalinsa bai kai wajenba saboda wani babban business da ya dauki hankalinsa kwana biyun nan. Smart kuma bai sanarma Uncle Yousuf ba dan yakan ɓoye wasu abubuwan gudun tada musu hankali. Muryar Daddy har rawa take wajen faɗin, “Aliyu yaya akai kasan wannan kai da kake anan?”.
Murmushi Smart yay masa, cikin shafa kai ya ce, “Daddy koyarwarka ce ai. A yanzu idanuna a buɗe suke akan duk wani motsin su Sulaiman da tawagarsa. Sannan Usman ya sake zame min cctv camara. Dan yanzu haka yana Nigeria yin wani aiki da ya shafi hakan ma. Sannan Uncle Yousuf shine jagoran tafiyar,..”
Da sauri Daddy ya dubi Uncle Yousuf. Murmushi yay masa ya kauda kansa shima. Smart yay dariya shima da cigaba da cewa, “Mu yanzu fatanmu Daddy kaje ka kwanta abinka ka huta. Karka damu da duk wani ƙulle-ƙullensu dan biye muke da su. Yanzu haka a daren jiya sunyi zama kanka harma da Abba. Sannan akwai kayansu dake hanyar shiga Nigeria. Kayane masu nauyin gaske da suka haɗa kusan kaso bibbiyu na dukiyarsu domin kawosu, dan mugayen kayan shaye-shayen ne kawai a cikinsu da in har suka samu shigar da su zasu samu maƙudan kuɗaɗe. Target ɗin mu yanzu muna zargin Sulaiman nada Company na sarrafa magunguna a ɓoye, sai dai bamu san a ina Companyn yake ba, shine muke bibiya domin mu tabbatar…”
Ji Daddy yay kamar ya saki kuka, hannayen Smart da Uncle Yousuf ya kamo a cikin nashi, sai ma ya rasa mizaice da su. Sai ga hawaye kawai na gudu a fuskarsa. Da ga Uncle Yousuf har Smart rikicewa sukayi. A take suka shiga jera masa tambayoyi. Sai ya sakar musu murmushi yana goge ƙwallar tasa da faɗin, “Kunga bafa wani abu bane. ALLAH yay muku albarka. Ban taɓa tunanin zanga irin wannan ranar ba a gareni. Domin na ɓata tsahon shekarun girmana a tunanin yanda zan ɓulloma wannan al’amarin ne. A duk sanda nayi hangen sako su Hussain a ciki sai zuciyata ta ƙi aminta da hakan, saboda su sunada rauni. Sannan har yanzu suna a kan dokin ƙuruciya ne ba komai suke kallo a mai muhimmanci ba. Aliyu kai ɗan halak ne, nagodama ALLAH da yasa ka zamo mijin Mawaddat, na kuma godema ɗan uwana da yay wannan haɗin alkairi. ALLAH yay muku albarka. Ya kare rayuwarku da ta ahalinmu gaba ɗaya. ALLAH ya ƙara ɗaukaka ku, ku zama abin alfahari da babu irinsu a wannan zamanin. ALLAH ya albarkaci rayuwar Aliyu ƙarami da takwarana Isma’il (Ra’is) da Kamaluddeen, yasa suji ƙanku fiye da yanda kuka jiƙanmu”.
Cikin rauni Smart da Uncle Yousuf ke amsawa da Amin. Smart na ƙara jin ƙaunar surukin nasa na ratsashi. Ga Uncle Yousuf Daddy ya juya. A hankali ya furta, “Nasha gaya maka Yousuf kaine babana a wannan matakin, narasa baba ne kawai a suna, amma ga babana a kusa dani…..”
Cikin katseshi Uncle Yousuf ya ƙyalƙyale da dariya. Sai kuma ya rungumesa da faɗin, “Oh oh Yaya ni Wlhy kunya kake sakani, ni dai ba sai kace komai ba. Karka manta fa kaine na tashi nakema kallo a matsayin mahaifi kai da aunty Khareema. Kun raineni tun bansan kaina ba. Kun gatantani tun baku san minene daɗin ƴaƴa ba. Wlhy raina fansa ne a wajen kare ku daga duk wani maƙiyi da zaice kune abin harinsa. Ni dai fatana ka cigaba da kwantar min da hankalinka kawai da mana addu’a. Sannan ka janye mana ra’ayin su ƴan biyun kamar yanda Aliyu yace shine kawai aikinka.”
Kasa cewa komai Daddy yayi, Smart dake saurarensu yana murmushi ya ɗan fesar da numfashi yana ɗan jujjuya camara ɗin. “Inaga a wannan gaɓar ya kamata Mawaddat ta fara aikinta. Dan haka zan duba abubuwan cikin camara ɗin nan tare da ita. Sai dai ina jin tsoron al’amarin ta dan bata da haƙurin kawaici ma abu, zata iya buɗe mana aiki da wuri wlhy”.
Yanda ya ƙare maganar cikin marairaicewa ya saka Daddy da Uncle Yousuf kwashewa da dariya. Dan kuwa suko suka san wacece Mawaddat. Daddy yace, “Aliyu kamar kasan abinda nake tunani kenan ALLAH. Dan Mawaddat yanda kasan zawayi haka take. Ballema ta ƙullaci Sulaiman ɗin a yanzu, dan bakaga yanda taima Dada bane ba ma fa. Abinda kawai zamuyi shine da zarar kun gama gani sai mu samu lokaci mu zauna da ita mu duka kafin na wuce. Sauƙin ma ga babanta da ya san matakan bida ita yanda ya kamata sai kaga tayi abinda ake so”
Murmushi kawai Uncle Yousuf ya keyi shi dai. Yace “Ku gama gulmarta duk sai na faɗa mata ai, dama kun mata wayo kun kawota nan. kai kaine za’a hana tuwo”… Yau maganar yana nuna Smart.
Dariya Smart da Daddy keyi, Daddy yace, “Sauƙin abinma kaine gaba-gaba wajen ƙullawar dan nayi recording.”
Smart ya kasa daina dariyar waɗan nan mutane. Komai nasu a sauƙaƙe cike da ƙauna da soyayyar juna. Suna ƙara masa ƙaimi akan ƙaunar ƴan uwansa shima…..
_______★
A ɓangaren Lulu tun fitar Smart itama ta fice a gidan. Asibiti ta nufa saboda maganar Smart dake cimata rai akan shi baya saɓa saiti. Haka kawai take jin tsoro a ranta, ita yanzu ta samu ciki kuma ai taga bonu. Yaushe ma yaronta yay ƙwarin hakan. Bawai bata son yara ba, amma dai tafi son ko zata sake haihuwa sai AA ya kai irin 5years haka. Yanzu kam tana ina zata fara haɗama kanta cakwakiyar nan, ga business ga rainon AA, ga fitinar ubansa, ga rainon ciki da hidimar ƙungiya dana aikinta. Ta samu ganin likita, babu wani kwana-kwana tace planning zatayi, amma su fara tabbatar da babu wani abu a jikinta, duk da dai a ganinta haɗuwa uku bai zama lallai a samu wani abu ba, to amma idan tai la’akari da farkon haɗuwar aka samu cikin AA sai hankalinta ya sake tashi taji ta kasa yarda da kanta. Doctor dai ta mata dukkan abinda ya dace sannan ta bata magani, acewarta a iya bincikensu mahaifarta fresh take babu komai. Amma ga magani tasha koda ma an samu akasi marar zata sake wankuwa fass. Daga haka suka saka mata abu a jiki ta dawo gida tana jin hankalinta a kwance. Ta iske har lokacin Smart bai dawo gidan ba. Dan haka ta ƙirƙiri aiki dan zama waje ɗaya ya isheta. Tsaff ta gyara gidan tare da musu girkin Nigeria yau. Tana kammalawa tai wanka, kayanta da ya rage ɗaya tak ta saka ta dawo falo ta zauna dan AA tunda suka dawo barci yake abinsa. Ta shagala a kallo ya shigo gidan da sallama hannunsa ɗauke da kaya. Bata motsa da ga inda take ba ta dai zuba masa ido, shiko nashi idanun na kallon gidan ne da yanda aka gyara shi, aka canja zaman abubuwa da yawa. Gyaran mace dabanne. Ya ayyana a zuciyarsa yana ajiye kayan hannunsa a hankali. Kusa da ita ya kai zaune cikin yanayin gajiya ya ke faɗin, “Madam ya gidan?”.
Baki ta tura da faɗin, “Ni ALLAH idan baka daina cemin Madam ɗin nan ba zamuyi faɗa ko kaima na saka maka suna. Sai kace wata tsohuwa?”.
“Oh da yarinya kike ɗaukar kanki, ai kin tsufa tunda gaki da AA. Nan da shekara ashirin zaki ga anzo fara miki gaisuwar uwar miji”.
Dariya ta ƙyalƙyale da shi, ta ce, “Kai kuma Baban miji ko”.
Murmushi yayi yana ɗan girgiza kansa. Sai kuma ya lunshe ido ya sake buɗewa a kanta. “Ina boss ɗin gidanne naji shiru?”.
“Barci yake, shiyyasa nake hutawa ta ai.”
“Ai yanzu ga baban shi ya dawo hutu ya ƙare”. Yay maganar yana kissing kuncinta da kwantar da kansa a kafaɗarta. A hankali ta sauke numfashi da lumshe idanunta itama. Dan zuwa yanzu duk yanda taso cigaba da riƙe kanta salonsa na barazanar tonata ne. Ƙarfin hali ne kawai da taurin kai irin nata. A hankali ta ce, “Yaya wasan?”.
“Alhamdullah bakin ƙi zuwa kallo ba”.
“To ni Wlhy ban iya kallon ƙwallo bane”.
“Sai ki fara koyo ai”.
“Zan ƙoƙarta in shan ALLAH kodan kai. Ni yanzu ma maganar da nake son maka shine jibi fa ya kamata mu koma”.
Batare da ya buɗe idonsa da ga rufen da suke ba ya ce, “Ina kenan?”.
A shagwaɓe ta ce, “Nigeria mana”.
“Uhhyim yin me?”.
Idanu ta zuba masa da mamaki, “Ya zakace yin me bayan kasan ayyuka na baro na taho nan, kuma ni da shirin sati ɗaya na taho ko kwana goma. Wlhy inada abubuwa masu yawa acan”.
Kaɗan ya buɗe idanunsa yana kallonta, tsahon mintina kamar bazaiyi magana ba sai kuma ya firzar da numfashi. Cikin deep voice ɗin nan nashi da babu wasa a cikin fitar sauti ta ya ce, “Mawaddat! Ke yanzu idan ance miki ki ƙara tafiya kibar mijinki sai ki tafi? Kiyi lissafi shekarar aurenmu ɗaya da wattani takwas kenan fa. Amma bamu taɓa zaman cikakken wata guda ba har yanzu. Idan ke baƙya jin damuwa da hakan ni gaskiya ina ji. Sannan haƙurina ya ƙare ina buƙatarku a kusa dani yanzu. Shekarunmu tafiya suke bakwai komawa baya ba, ko sai ƙarfina ya ƙare sannan zaki fiskanceni a gaɓar da bazan iya komai a gareki ba. Na waiga ma na ganku a kusa da ni farin ciki nake ji. A yanda nai wasa a fili yau kowa yasan ina cikin farin ciki mara misali, aure ibada ne fa bawai son zuciya ba ko ra’ayin kanka a yanda kaso tafiyar da shi. Dan haka maganar komawa na soke shi, ba yau ba, ba gobe ba babu ma rana kawai at all. Dan haka karma ki sake mun maganar data shafi hakan ranmu zai ɓaci ne kawai”. Ya miƙe fuska a tsuke ya bar falon zuwa bedroom……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣5️⃣
…….Da kallo kawai ta bishi zuciyarta na wani irin rawa da mamakinsa. Gaba ɗaya ya juye mata a kammanin da ta sanshi tun farko na dakewa da rashin son ɗaukar raini. Gaba ɗaya sai taji ma shakkarsa ta shigeta. Kusan minti uku tunaninta ya fara zurfi sai kuma ta miƙe, dan ganin ɓacin rai a tare da shi kuma duk sai take jin itama nata zuciyar babu daɗi. Bedroom ɗin ta shiga da sallama ƙasa-ƙasa, inda yake tsaye yana saka bathrobe a jikinsa ta nufa, dan har ya cire kayansa. Sallamar kawai ya amsa mata batare da ko kallonta yayi ba harta iso gabansa. Fuskarsa da ke kicin-kicin ta zubama ido, ganin bazai kalletan ba yasata kai yatsanta manuniya ta ɗan takaleshi a kafaɗa. Kautar da jikinsa yay, ta ƙara lakatoshi a hannu, ya sake kaucewa kamar wani ƙaramin yaro, sai kawai ta matsa ta rungumeshi ta baya ta ɗora kanta a saman bayansa tare da zagayo hannayenta saman cikinsa tana wasa da igiyar bathrobe ɗin kamar zata kwance. Idanunsa da ya lumshe saboda jinta a jikinsa ya ɗan ƙanƙame jin ta zagayo hannunta saman cikinsa, a hankali ya firzar da iska yana cije lip ɗin sa na ƙasa kaɗan da ƙoƙarin yana ƙoƙarin zame hannun nata amma sai ta sake ƙanƙamesa.
“Fushi kayi?”.
Ta faɗa a hankali. Shiru kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya ɗan sake sauke numfashi da kama hannun nata ya zagayo da ita gabanshi. Mayatattun idanunsa ya zuba mata kamar yanda itama take kallonsa cikin tsakkiyar ido. Gira ta ɗan ɗaga masa tare da kanta, “Fushin dai?” ta faɗa tana kai yatsarta ƙirjinsa a saitin zuciyarsa ta shiga zagayawa da faɗin, “To ki huce hajiya zuciya”.
Harararta yay da buge mata hannu yana sake ɓata fuska kamar wani AA. Sai kawai ta ƙyalƙyale da dariya da faɗawa jikinsa ta sake rungumesa.
“ALLAH in kana shagwaɓa kamar AA najin yunwa fa”.
Duk yanda yaso cigaba da riƙe kansa ya kasa. Murshi yayi yana ɗan lumshe ido da dungure mata kai, sai dai baice komai ba. Dan haka ta fara masa cakulkule. Dole ya fara dariya da ƙoƙarin janye jikinsa amma taƙi barinsa, sai ma baya yake tana binsa har suka faɗa saman sofar ɗakin. Bata daina ba duk rokon da yake mata sai da ta tabbatar ya jigata sannan ta barshi tare da faɗawa kansa suna dariya su duka.
“ALLAH ke muguwa ce”.
Ya faɗa yana ja mata hanci. Amsa ta bashi da “Ai kai ka koya min dan kaine malamin koya mugunta ma”. itama tana dungure masa kai. Sai suka sake ƙyalkyalewa da dariya.
“Kin fara nauyi ALLAH, ɗaga ni karki fasa min ciki”.
Fuska ta ɓata da duban kanta, sai kuma ta hararesa da faɗin, “Ta ina na ƙara ɗin? Ni ALLAH bana son sharri”. Kallo ya bita da shi irin a ɗan ɗagen nan, sai kuma ya nuna mata yana gimtse dariya. Inda ya nuna ɗin ta kalla. Da sauri tace “ALLAH zai saka min” tana kai masa duka da filo. Ƙoƙarin riƙewa yake tana dariya da faɗin, “Daga faɗar gaskiya. To shikenan na yarda baki ƙaraba. Ƴar ƙanwata na nan yanda take ƴar sawalwala abinta cas-cas”. Sauka tai da ga jikin nasa ciki nuna irin nayi fushinnan, shima sai ya miƙe da sauri ya riƙota tare da ɗagata gaba ɗayanta suka fice a ɗakin. Tana zille-zille da faɗin ya sauketa bai kulata ba ya fita ta baya inda swimming pool ɗinsu yake. Direta yay a bakin ruwan ya cire bathrobe ɗin jikinsa yay hanging a kan ɗan ƙarfen da aka saka domin hakan kawai dama. Da sauri ta kauda idanunta da ga kallonsa, dan har yanzu ta kasa iya daina jin kunyarsa, duk da bawai haka nan yake ba akwai ƙaramin boxer jikinsa bazata iya jurar kallon nasa ba kai tsaye a haka. Shima komai baice mata ba sai murmushi da ya saki kawai, cike da kwarewa yay tsalle da sufa irin na masu wasa da ruwa cikin ruwan. Yanda ya fantsama ciki sai da ruwan ya tarwatso mata a jiki har a fuska. Fuskar ta kwaɓe tana kallonsa kamar zatai kuka, shi baima san tana yi ba sai da ya kai ƙarshe zai juyo ya kula. Dariyar mugunta ya kwashe da shi, sai kuma yay ƙasa cike da kwarewa ya sake dawowa gabanta ya miƙe tsaye yana dariyar da ɗibar ruwan a hannu ya sake watsa mata a fuskar. Lulu ba haƙuri idan akai saita rama. Hannu takai itama zata ɗibo danta rama ya fisgota ta faɗo ciki. Kokawa suka fara a ruwan yana kunnata da dariya, sai kuma yay mata gwalo yay ƙasa cikin ruwan. Itama da sauri ta nutse ciki ta bisa saikace wasu kifaye…
Sun jima a cikin ruwan suna nishaɗin su kafin suka fito saboda tunawa da AA shi kaɗai a ɗaki. Bathrobe ɗin da yazo da ita ta saka, sannan taje ta ɗakko masa wata shima. Tun shigarta ɗakko masa rigar ta samu AA ya tashi, dan haka bata zauna jiransa ba ta juya ciki. A ɗakin ya sameta tana cirema AA kaya, yana ganin shi ya shiga miƙa masa hannu dan yanzu ya daina masa ƙiwa. Shima cikin farin ciki ya ɗauki abunsa yana mai sumbatarsa da faɗin, “Oh oh Baban Ammah ya tashi kowa ya ɓoye kayansa kafin a cika musu aiki”.
Cikin dariya Lulu tace, “Aikam dai, dan yanzu zai fara haɗa gwaramar tasa”.
“Ai ke ya gado, dan Uncle Yousuf ya cemin kema kina ƙarama hummm”.
A shagwaɓe ta ce, “Shi Uncle You ɗin ya faɗa, ni dai ALLAH babu ruwana salaha da ni, sai dai kai dan dama Ammah tace tasha rashin jin ka”.
Shima fuskar ya ɓata da faɗin, “Sharri ba haushi zanji ba ai” daga haka ya nufi bedroom da AA a kafaɗa domin yimasa wanka. Dan yanzu in har yana gida kusan komai shikema yaron, acewarsa yana koyane koda ta haifo ƴan uku basai sunje neman Nanny ba. Takan hararesa kawai idan yace hakan…..
★ Zaune suke a wajen cin abinci yana cin abincin da tai masan idanunsa a lumshe alamar dai yana jin daɗin sa, itako sai murmushin farin ciki takeyi. Dan a yanzu babu abinda ke sakata a farin ciki sama data gansa cikin farin ciki. Batai zaton zaici abincin haka da yawa ba, sai gashi ko yaci sosai har yana faɗin jikinsa yay masa nauyi. Bayan ya kammala ta gyara wajen suka koma falo. Zama yay yana wasa da AA ita kuma ta kwashe kayan da ya shigo da su zuwa ciki, na kitchen kuma takai kitchen. Sosai taji farin cikin ganin kayan sakawa ne ya siya mata, sai turarruka na mata masu daɗin ƙamshi duk da tazo da su khumra da turarrukanta abinta. Sai kayan kwalliya da batazo da su ba, shima AA an saya masa nasa. Tana cikin kwashe kayan taci karo da camara. Tsai tai tana kallo da jujjuyata a hannu, sai kuma ta ajiye cikin taɓe baki ta cigaba da gyara kayan. Sai da ta kammala tsaff ta ɗauka camara ɗin ta koma falo da ita. Kwance yake a ƙasan carpet yana waya da Ahmad, AA na gefensa yana wasa da kayan wasansa, yanda ya nutsu sosai ya tabbatar mata da magana suke mai muhimmanci, dan haka ta kai zaune Camara ɗin a hannunta tana kallonsa shi da AA ɗin cike da jin farin cikin su ɗin duk nata ne fa. Abinda ya ɗan fara jan hankalinta ga wayar tasa shine kalmar daya ambata cikin yanayin ɗan ƙaraji har yana tashi zaune. Sosai ta zuba masa idanu, yayinda shi kuma ya cigaba da faɗin, “Kaga Ahmad relax please. Karka ruɗar da kanka, ni dama nasan dolene wannan binciken ya tono mutane da yawa a ciki, aiba abin mamaki bane ba hakan karma ka tada hankalinka a banza. Yanzu abinda zamuyi shine dole mu tafi mataki na biyu, wato plan B.”
Cikin matsanancin ruɗani da ga can Ahmad ya ce, “Dole ne hankalina ya tashi Aliyu. Mahaifin aunty Khadijah fa! Kasan kuwa yanda nake ganin mutunci da kimar mutumin nan, amma ace har da shi a cikin mutanen nan. Kasan kuwa irin muggan miyagun kwayoyin da yaron nan ya sanar min ana saidawa a pharmacy ɗin nan! Ban taɓa sanin haka ƙasar nan tamu ta lalace da rashin doka da bin ƙa’ida ba sai yau. Innalillahi wa-inna ilaihiraji’un”.
“Humm Ahmad kenan kana wasa da mutanenmu. Abinda yasa kake ganin irin waɗan nan abubuwan abin mamaki saboda rayuwar daka tashi ne. Amma mu da aka haifa a getto eria muka rayu a ciki munsan irin waɗan nan abubuwan fiye da yanda kake zato, kawai dai mutum dan baida ƙarfin ɗaukar matakine shiyyasa. Ni dai abinda nake so da kai yanzu dolene fa ka sake ƙara ɓoye kanka, dan ko Yaya Hameed da Uncle Yousuf ban san susan da hannunka a ciki, shiyyasa ma kaga nace Uncle Yousuf ɗin yabar komai a hannuna shima saboda suma suna huɗɗa da mafi yawan manyan ƙasar, zamu iya zuwa gaɓar da al’amarin wani zai girgizasu su buɗe mana aiki”.
“Hakane Smart na fahimceka yanzu, kuma in sha ALLAHU zamu basu mamaki, tabbas mune matasa ya dace muyi hanƙoran gyara ƙasar nan tamu akan wannan mummunar safarar dake cigaba da yaɗuwar gurɓatamu tamkar wutar jeji a kasarmu, in ba haka ba sai anzo lokacin da babu wani matashi da zai iya amfanar kansa balle wani ko ƙasar, zasu cigaba da mana illa ta hanyar dafe madafin iko su barmu da raɗaɗin shan miyagun ƙwayoyin da suke mana safara mu kuma muna sha da tunanin rage raɗaɗi, wlhy Smart naji na tsanesu, natsanesu, su azzalumai ne…..” Kukan da ya tahoma Ahmad ya hanashi ƙarasawa, shiru kawai Smart yay yana saurarensa shima zuciyarsa na ƙuna. Tuni idanunsa sun gashe zuwa jajur. Yana jin raɗaɗi fiye da wanda Ahmad yake ji, tun yana yaronsa ya tsani shaye-shaye, baya son yaga anayi, yana jin ciwo matuƙa idan yaga matashi ya lalata rayuwarsa da shaye-shaye, shiyyasa cikin ƙanƙanin lokaci al’amarin Lulu yay tasiri a zuciyarsa. Da ƙyar ya iya furta, “It’s okay Ahmad. Kuka bashi ne magani ba, aiki tuƙuru domin ganin mun karya su. Sannan inaga dolene zamuyi amfani da ƙungiyar Mawaddat a wannan gaɓar domin tattarro hankalin matasa dan wannan aikin yana son taron dangi ne. In ba hakaba zaƙulosu da muka ɗauka ɗammarar yi bazai magance mana matsalar ba tunda zasu iya sayen hukumomi da kuɗi kasancewar wasu a cikinsu suma ruɓaɓɓune”.
“Tabbas haka ne nima nayi wannan tunani, kuma na yarda da shawarar nan naka. Sai dai yanzu ban san yaya zamuyi ba tunda kaga ita tana nan”.
Cikin ɗan ɓata fuska da kallon Lulu ta gefen ido ya ce,,……✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣6️⃣
…….“Ni kuma gashi gaskiya bazan iya baku Matana ba yanzu dan kaima dai kasan ango nake”.
Dariya Ahmad ya kwashe da shi da faɗin, “Ɗan iska shegen sama. Banza ta faɗi ko anata kwasar romon dimakuraɗiyya. Sai kaita riƙo ai ko tana nan zata mana aiki”.
“Shegen sa idon ka dai a kanka zai ƙare. Sai dai fa daga nan ɗin dan mai kawo min mata Nigeria yanzu ban gansa ba”. Ya ƙare maganar yana kashema Lulu dake kallonsa ido. Kanta ta ɗauke tana ɗan murmushi da harararsa. Dan ita ta ƙagara ya kammala wayar ya mata bayani. Sun sake tattaunawa sosai da Ahmad ɗin kafin suyi sallama. Yana yanke wa kiran Uncle Yousuf na shigowa. Tashi yay yabar falon ma gaba ɗaya, Lulu ta bishi da kallo cikin jin tsarguwa. Bai jima ba sai gashi ya dawo. Ganin yanda ta turɓune fuska ya sashi zuba mata ido.
“Lafiya kuwa Madam?”.
Baki ya taɓe da ɗauke kanta gefe. A hankali ya kai zaune kusa da ita yana mai kamo fuskar tata. “Please miya faru kar kiyi fushi mana.” harara ta sakar masa da buge masa hannu tana son tashi, yay saurin riƙota ta faɗo jikinsa. Rungumeta yay da ƙyau ta yanda bazata iya tashin ba. Cikin tallafo kanta da ɗaura goshinsa a saman nata ya ce, “Please Baby luv, kin san fa da fushinki gara kawai a tada yaƙin duniya na uku. Faɗamin minene?”.
“Ba kai bane kake ta wani ɓoɓɓoye abu dan kar naji”.
“Haba ni na isa. Kikama san Aliyu ciki da bai ɗinsa balle abinda ke a zuciyarsa. Dama fa zan yi maganar dake”.
“Babu wani ban yarda ba. Bayan tun randa mukazo kaketa wani magana da Ahmad a cuccure, hakama idan Uncle Yousuf ya kiraka sai ka koma gefe ko Daddy”.
“To yi haƙuri bazan sake ba. Bani ɗan lokaci yanzu zan miki bayanin komai dan kema kina daga cikin tawagar ai. Dama ba’azo gaɓar da naki aikin zai fara bane kawai shiyyasa. Haɗamin coffee yanzu ina zuwa”.
Babu musu ta miƙe zuwa kitchen, ya bita da kallo har sai da ta shige sannan ya tashi yana sauke ajiyar zuciya. Bedroom ya shiga, babu jimawa ya fito ɗauke da laptop a hannu da Flash drive kusan huɗu. Centre table ɗin falon ya jawo gabansa sosai yana kaiwa zaune da zube kayan hannunsa, sai lokacin idonsa ya sauka akan camara ɗin data ɗakko. Ɗauka yay ya ajiyeta a gefe yana girgiza kansa, sai gata ta fito ɗauke da ƙaramin tray da coffee 2cups sunata turiri.. gefensa ta zauna tana ajiye masa nasa gabansa itama ta ajiye.
“ALLAH yay miki albarka”.
Ya faɗa yana ƙoƙarin saka flash a jikin Laptop ɗin. Cikin jin daɗi da farin ciki ta amsa masa. Dan a duk lokacin da yace ALLAH yay mata albarka tana matuƙar jin kanta on top ne. Sai da ya gama saita komai ya kalleta. “Ina son ki nutsu sosai dan maganar da zamuyi mai matuƙar muhimmanci ce”.
Kanta ya jin jina masa da sake maida hankali garesa sosai. Cikin nutsuwa shima ya fara mata bayani ta yanda zata fahimta tun daga randa Daddy ya fara aiki a maikatar da Alhaji Sufi Garko ke shugabanta, wanda a dalilin haka ne ya ja Daddy a jikinsa, a maimakon aikin gwamnati ya maidashi akan harkokin kasuwancinsa. Yanda abubuwa suka dinga tafiya har zuwa sanda kuɗi suka ɓata da shiga jikinsa da Sulaiman ya farayi ta hanyar nuna masa zai taimakesa da kasuwancin da suka fara tare har zuwa sanda ya fahimci abinda ke cikin business ɗin da haduwar Daddy da mahaifiyarta, da abinda ya faru a dalilin aurensu, fyaɗen da Alh. Sulaiman yay ma Sultana da yanda Daddy ya tayashi ɓoye sirrin zamansa da mahaifiyarta, rasuwarta, mutuwarta, ɗauketa a Nigeria har zuwa girmanta, shigowa rayuwarta da yayi dama kamun da Alh. Sulaiman yay masa har zuwa aurensu da buɗe musu ciki da Daddy yayi akan komai da dalilinsa na ɓoyewa. Yanayi yana nuna mata abubuwa a laptop ɗin nashi, yawanci duk wayoyin barazana ne, da wasu harƙalloli tsakanin Daddy da Alh. Sulaiman ne, dama hotunan abokan da sukai huɗɗar kasuwanci da Daddyn ya adana matsayin hujjar da ya dinga tsorata su Alh. Sulaiman da tawagar su Nakowa da ita. Tunda ya fara Lulu ke kuka na tashin hankali, har takai AA ma ya fara kuka sai da Smart ya ɗaukesa ya ɗaura a cinya. Jikinta tsuma yake matuƙar tsuma, idanunta sun masifar kumbura saboda kukan da taci. Cikin damuwa ta ce, “Na cikin camara ɗin ma dan ALLAH ka nuna na gani”.
“Ba yanzu ba”.
Ya faɗa yana jawota jikinsa ya rungume cikin lallashi. Sai ta sake tsage masa da kuka. Muryarsa a raunane shima kamar zai saki kukan ya ce, “Please mana ya isa kukan haka kinji, mugodema ALLAH tunda babu abinda ya faru da shi. Duk da ina ji a jikina da saka hannun Sulaiman a zuwan Felix gareki, hakama su Alace da Luna da suka koya miki shaye-shaye ina zargin sakasu akayi mawaddat duk da dai bani da tabbaci.”
Kanta ta sake turawa a jikinsa tana kuka mai cin zuciya. Duk sai hankalin Smart ya sake tashi. Dole ya rufe laptop ɗin ya maida hankali a lallashinta da bata baki. Duk yanda taso suga abinda ke a cikin camara ɗin a yau yaƙi yarda. Da yaga ta damu sai yace mata dole sai an kwashe abinda ke cikinne zuwa flash shiyyasa. Badan ta yarda da shi ba ta haƙura, sai dai ta ɗauka waya tai kiran Daddy. Yanda yaji tana kuka shima sai hankalinsa ya tashi, cikin ruɗewa ya shiga lallashinta da tabbatar mata tayi haƙuri zuwa gobe zai shigo birnin London shi da Uncle Yousuf. Hakan ya ɗan sakata jin sassauci, dan babu abinda tafi buƙata a yanzu sama da taga Daddyn a kusa da ita. So take ta sake tabbatar da babu abinda ya samar mata shi. Uncle Yousuf ma ya amshi wayar ya lallasheta, hakan ya ɗan ƙara saka mata jin sauƙi, bayan ta yanke wayar ta shige jikin Smart tana hawaye. Murmushi yay yana mai ɗagota, cikin zuba mata idanu ya kai lips ɗinsa kan nata a hankali. A nutse ya canja yanayin nasu zuwa wani abu daban, babu kunya a falon akai yaƙin ƙasa-da-ƙasa, sai dai ƙura ta lafa kuma ta koma jin nauyi. Shi kuma yana mata dariya da tsokana wai dama abinda take so kenan ashe. Itama dai yanzu ta zama babbar mayaƙiya. Tashi tai ta bar masa falon bayan ta gama mimmitsinesa da bubbuga masa filo. Da kallo ya bita yana mai jin ƙarin ƙaunarta mai faɗi da girma na sake mamaye sa tako ina. Da ga ƙarshe ya miƙe da ƙyar ya bita bedroom ɗin. Bathroom ya nufa inda yake jinta sukayo wankan tare. Shine ya koma falon ya ɗakko AA da ke barci. Suma dai kwanciyar sukai domin hutawa ransu…..
*_NIGERIA_*
Sau biyu ana ɗorata amma ƙashin ya gagara zama saboda tanada ƙiba, gashi a cinya ta karye. Su kansu malaman asibitin lamarin neman fin ƙarfinsu yake. Ƙaninta dake tsaye kan lamarin nata ne ya yanke shawarar su nemo masu ɗorin gargajiya. Dan mijinta tunda yazo zuwan farko asibitin yaji irin sambatun da takeyi da tona ma kanta asiri ita da aminiyar tata da ayanzu kowa ke kira da Dodo ransa yay masifar ɓaci. Ashe itace ta rabashi da matarsa mai sonshi dan ALLAH tun bashi da komai, sannan ta rabashi da manyan ƴaƴansa da sam yanzu ko kallon arziki bai musu da ma danginsa. Hatta da karatunsu bai saka hannu ba gashi yanzu duk ALLAH ya tallafesu sun samu ayyukansu. Ranar yayi kuka da hawayensa da yin dana sani. Yana zaune da matarsa lafiya ƙyale-kyalen Naqiba da suka haɗu a wajen aiki ya kwashesa har yana kushe matarsa akan bata iya komai ba sai gidadanci saboda kawai batai zurfi a ilimin boko ba. Shagalin biki akai na alfarma lokacin ya zubda kuɗi tare da sakata a danƙareren gidansa da ya gama gini. Itace ta gaban mota idan zai fita, itace ta zuwa jahohi idan aiki ya kaisa, acewarsa itace mai ilimi. Duk da bawai wani mahaukacin kuɗi ne da shi ba yanada rufin asirinsa dan har Saudiyya yaje kusan sau uku, kuma duk tare da matar son nasa Naqiba. Yakan je Dubai kuma saro kaya a yanzu haka, dan yanada manyan shaguna a cikin kasuwar kwari. Yakan yima Naqiba abu sau sama da goma kafin yayma matarsa da ƴaƴansa, a haka har suka haihu ɗaya da ita, dan Maheer kawai ta haifa sai mace ita kuma ta rasu tun tana 3years….
An sake ma Hajiya Naqiba ɗorin gargajiya da taci uwar azaba harda sumanta. Bayan farfaɗowarta ne ta cigaba da sambatu kamar zautacciya. A wannan halin su Abba da sukazo dubata saboda a gidansa ta samu matsalar, yana ta son zuwa sake dubata tun randa suka kawota asibiti tashin hankalin Ummah ya hana shi. Sai yau ne yaga ya dace yazo kar ai abin kunya shine ya kwaso su Abdull suka zo. Anan ne kunnensu ke jiye musu sambatun Hajiya Naqiba da ke fallashe sirrinsu. Ba Abban kawai ba hatta su Mubarak ji sukai ƙasa na neman kasa ɗaukarsu. Bakin Hajiya Naqiba bai mutu ba sai da akai mata alurar barci mai ƙarfi. Tuni Abban ya baro ɗakin ko sallama bai iya yima danginta dake cike da ɗakin suna faman mata ALLAH wadai ba. Cikin sauri yaransa suka take masa baya. A wannan tashin hankalin suka dawo gida, sun iske Yayan Ummah Jibirin ya sake zuwa da wasu malaman yau ma. Sai dai suna jira Abban ya dawo a tunkari Ummhn.
Duk hayaniyar da akeyi Umma na jiyosu da ga falonta, sai dai furucin Abba yasa a yanzu bata iya fitowa ko tsakar gida, dan ya tabbatar mata idan ta sake fitowa ta firgita masa iyali batare da shi yace ba a bakin aurenta. Wannan kalma na ɗimautata a duk sanda ta sake maimaita kanta a ƙwaƙwalwarta. A cikin abinda bai wuce sati guda ba duk tayi wata irin firingau-firingau da ita. Tai muguwar rama kamar mai cutar sida. Kuka kam idanu sun daina sai dai na zuciya. Tunda take ko’a labari bata taɓa sanin akwai makamancin irin tashin hankalin nan nata a duniya ba. Ita a yanzu ma neman hanyar zuwa ga malamin da yay aikin take ya karya shi amma babu hali, tsakar gida ma ya gagari mutum balle ƙofar gida har akai ga shiga mota. Abincin tana cinsa ne kawai dan tsoron mutuwa. Amma badan yunwa ba. A duk sanda ta jiyo muryar Ammah dai ta fashe da kukan baƙin ciki na tsananin jin kishi. Tana jin raɗaɗin tayaya za’ai ace Ammah taci nasara a kanta kenan? Itace fa Yahanasu mai yawan ƴaƴa maza a gidan fiye da kowa, ƴar uwar mai gidan jininsa, tafi kowa yawan ƴaƴa, ita ta fara haihuwa a gidan, tanada power ɗin juya miji a tafin hannunta koda daga baya zai suɓuce mata zata sake nemo hanyar riƙosa. Kowa a waje gani yake itace ke juya gida da miji, amma a kullum sai Hafsatu ta zama sanadin rusa mata plans nata. A kowace safiya tana ji kamar ta kashe matar nan ko zata ji sassauci na zafin tsanar da take mata. Kuka irin mai ƙona zuciya ɗin nan ya suɓuce mata, sai dai babu ɗigon hawaye a cikin idanun sai zafin zuciya da gwara ma kaita hawayen……..✍️
_🥱🥱Jiya kunji shiru ko. Ina nan na dage muku da typing ne nima na ƙagara mu gama🚴🚴._
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣7️⃣
…….A gidan Alhaji Garko kam ALLAH ya sauki amarya lafiya, ta silloɓo ƴan biyunta duk maza har guda biyu masu kama da Baba Garko da ƴan uwansu. Farin ciki a wajen Baba Garko da ma’aikatan gidansa ba’a magana. Babu ko ɗar balle jin kunya ya ɗaga waya yay kiran Dada a farko. Rabon da ya kirata a waya harta manta a rayuwarta, duk da halin da take ciki jikinta har rawa yake wajen ɗauka. Dan addu’a take a ranta ALLAH yasa baƙar dagar ce ta mutu ita da cikin. Sai dai me tana kaiwa kunne kalma ta farko da ga bakin mijin nata, abin sonta da sukai ƙuruciya ga su a tsufa tare itace, “Alhamdullahi ALLAH ya sake azurtani da yara biyu MAZA masu kama da ni kamar sauran ƴan uwansu. Sai ki shirya kayan tarbar sabbin ƴaƴa Hajarah”. Da ga haka ya yanke kiran kamar dama da gayya yayi, hakan yay dai-dai da tsayawar numfashin Dada da tunda ya fara maganar yake fita dama a fisge. Yaraf ta sulale a wajen ta zube babu numfashi…..
(🥱DADA team sai ku kai ɗauki🚴).
_________★
Kamar kullum pharmacy ɗin cikin hada-hada da kai-kawon mutane yake. Dan babban pharmacy ne da duk kalar maganin da kake nema ko kayan anfani da ya shafi lafiya zaka sameshi. Ga shi akan babban titin da mutane ke yawaita kai-kawo sosai kuma. Ba sayen ɗai-ɗai kawai suke ba har sari suna badawa wa ƙananun camix ma. Banda ɓoyayyun masu amsar miyagun kayansu da ko yaran shagon ba kowa yasan ana harƙallar ba sai amintattun ciki da masu lura, sai dai kosun luran babu damar magana dan anfi ƙarfinsu.
Duk da safiyace akwai mutane sosai musamman masu sari. Basu wani damu da jin dirar motocin ƴan sanda ba a ƙofar pharmacy ɗin kowa ya cigaba da abinda yake yi. Sai dai me motocin ƴan sandan na gama dira ta NDLEA suka dira suma har mota uku. Sai a lokacin hankalin mutane ya fara dawowa jikinsu, sai dai kafin yin wani yunƙuri jami’an gaba ɗaya sun rufe ƙofar pharmacy ɗin. Sauran kuma sun afka ciki. Gaba ɗaya mutanen ciki an tattaresu zuwa mota, hakama ma’aikatan an tisa ƙeyarsu cikin store ɗin wajen wasu kuma cikin pharmacy ɗin. Duk tambayar da suke akan su mi sukayi babu wanda ya basu amsa. Jikin Manager ɗin wajen har rawa yake wajen ƙoƙarin kiran layin oga kwata-kwata ya sanar masa.
Duk da hankali Alhaji Sadi Dikko Baduku ya tashi da jin wai NDLEA a pharmacy ɗin nasa sai cikin rashin damuwa da gadarar masu arziƙi ya buƙaci yaron nashi ya bama ogansu waya. Cikin jin ƙwarin gwiwa Manager ya nufi wanda yake ƙyautata zaton ogan nasu ne ya kai masa wayar. Kallon sama da ƙasa mutumin yay masa tare da daka masa tsawar da sai da ya zabura. Ba Manager ba hatta shi kansa Alhaji Sadi Dikkon sai da ya zabura. Mamaki da al’ajabin wane ɗan iska ne wannan ya sashi yanke kiran, da sauri ya shiga neman shugaban hukumar NDLEA na Kano baki ɗaya, sai dai har wayar ta gama ring ba’a ɗauka ba. Sake kira yay aka danna masa busy alamar an yankesa. Anan ne fa hankalinsa ya fara tashi, da sauri ya shiga neman number Hon. Nakowa…..
*_UK_*
Kasancewar yau bashi da wasa suna nane a gida suna zubama juna taɓara. A yanzu haka zaune Lulu take gaban Mirror Smart tsaye a bayanta wai yana mata gyaran gashi. Yayinda AA yay busy a ƙasa da kayan wasansa cikin kuzari da lafiyar da ALLAH ya bashi. Dan yanzu haka Alhmdllh yana miƙewa har ai taku ɗaya zuwa biyu musamman idan idanun iyayen basa kanshi. Idan ma sun gansa sai ya koma ya zauna kamar dai yanda akasan yara masu koyan tafiya kanyi na rashin son a musu ihu yayinda suka miƙe. A hankali Lulu da ke kallon hotunan Smart a waya ta ɗago idanunta jin kamar ya daina motsa hannun nasa a saman kan nata. Cikin mamaki ta ɗan waro idanunta da faɗin, “Lafiya kuwa? Tunanin mi kakeyi haka?”.
Shiru babu alamar Smart ya jita, dan sosai yayi zurfi a tunanin nasa. Wayar ta ajiye tare da juyowa tana fuskantarsa, sai da ta riƙo hannunsa cikin nata ne ya sauke ajiyar zuciya. Hannun nasa taja zuwa wajen gado, babu musu ya bita. A bakin gadon ya kai zaune, ita kuma ta tsugunna a tsakanin ƙafafunsa hannayenta dafe a cinyoyinsa suka zubama juna idanu. “Mike damunka haka kake irin wannan tunanin Mr A?”.
Murmushi yayi a karo na farko, dan ya fahimci a kwana biyun nan bata iya kiransa da Aliyu kamar yanda take yi, ya ɗa furzar da iska kaɗan da kai hannu ya gyara mata gashin da ya sakko mata a gefen ido. A hankali ya furta, “Ba komai fa tunaninki kawai nake yi”.
Hararsa ta ɗan yi cikin girgiza kai, sai kuma ta marairaice fuska kamar zatai kuka. “Ina kusa da kai ne zakai tunani na. Ni ban kai na san matsalarka ba ko?”.
“Ke kikafi kowa cancantar sanin matsalata ai Baby luv”.
“Ban yarda ba tunda gashi ka kasa gaya min. Ni kuma duk sirrina babu wanda baka sani ba”.
Murmushi ya sake sakin mata da ɗan lakace hancinta. “Nima ai duk kin sani. Dan babu wanda ya kaiki sanin Aliyu a yanzu ciki da bai ɗinsa.”
“Ni ban yarda ba”.
“To mi kike son ji?”.
“Damuwarka”.
Hannunta ya kama tare da ɗagota ya zaunar a saman cinyarsa. Sai ya rungumeta sosai yana sauke ajiyar zuciya. Kusan minti ɗaya suna a haka sannan ya sassauta mata yana kwantar da kansa a kafaɗarta. “Baby luv abubuwane suna neman yin yawa a tsakanin nan. Na fahimci sam gidanmu babu kwanciyar hankali ga kowa musamman ma Abba da Ammah. Suna ɓoyemin ne kawai amma lamarin Ummah na damunsu. Nima da nake anan ɗin yana damuna, shiyyasa nake jin da inada dama zanje Nigeria a tsakanin nan gaskiya. Ga batun mutumin nan, nasan hatsabibine bana wasa ba, zai iya bin hanyoyi da yawa dan ganin ya cuta mana.”
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, sai kuma ta saki murmushi da shafa fuskarsa, wasa ta cigaba da yi da gashin ƙasunbarsa a hankali. “Humm ni dai ka kwantar da hankalinka. Na farko dai batun wata Umma ma ka ajiyesa gefe ita ta jama kanta damuwa da ita baida wani amfani. Na biyu mune ya kamata mu kwantarma da Abba hankali shi da Ammah dan suna damuwa ne saboda abinda duk ya faru a kammu akayisa. Sulaiman kuwa shi ba komai bane a yanzu takansa ma yakeyi. Amma kamar yanda ka faɗa kam zai iya yin komai da ga sanda ya farga ruwa ya ƙare masa. Dan haka komai yana buƙatar ayisa cikin gaggawa a yanzu gaskiya”.
“Kema kinzo da shawara kam. Sai dai kin san kamashi a yanzu kai tsaye bazai yiwu ba duk da muna da hujjoji”.
“Eh hakane, muna buƙatar gaɓa. Ma’ana a kamashi cikin wani laifi dumu-dumu irin wanda baida mafitar nan. Wannan shine zai sa a cigaba da zaƙulo laifukansa na ɓoye. Shiyyasa ka daure ka barni na koma Nigeria. Aikin nan yana buƙatar fuska da fuska ne fa”.
A take fuskarsa ta tsuke, babu alamar zai ce komai. Kansa ta ɗaga da ga kafaɗarta tana mai zuba masa idanu. “Wai kai ance maka zan gudu ne. Ina fa gama abinda nakeyi zan dawo ALLAH kuwa. In dai gudu ne kasa a ranka ka ƙaremin nawa yanzu babu sauran wajen ɓuya. Idan ma nace zan barka ai Uncle Yousuf da Daddy sai sunyi farfesuna koma su tauneni ɗanya. Kasan irin matsayin da kake da shi kuwa yanzu a gidan mu. Ai ko Ummita dana sani a baya-bayan nan defender ɗinka ce ta gani kasheni.”
Kallonta kawai yake shi dai, kafin ya samu damar cewa wani abu kira ya shigo masa waya. Ita ta miƙe zuwa mirror ta ɗakko. Gannin Daddynta ne ta ɗaga tana kaiwa kunne.
“My Son!”.
Daddy ya faɗa daga can. Cikin ɓata fuska tamkar tana gabansa ta ce, “ALLAH ya soni nima ina da Ammah da Uncle You da Abba da Mommy, ga Baba Garko”.
Sosai Daddy ke dariya. Ya ce, “Oh oh irin wannan gori haka Mawaddat. To ai ALLAH yasa ma Baba Garkon nawa ne ɗan sammiki nayi. Kinga sai ki ƙarata da iyayenki nima ki barmin nawa da kuma yaro na”.
Dariya tayi itama da faɗin, “Ai nafa bar maka Daddy ku ƙarata.”
“To shike nan ƴar albarka. Ki faɗawa mijin naki gamu nan tafe in sha ALLAH. Ina fatan dai yana gidan?”.
“Lah Daddy wai nan zaku zo? Dama kana London”. Ta ƙare maganar cikin shagwaɓa. Murmushi Daddy yayi da ga can har tana iya jin sautinsa. “A’a yau dai zamu shigo, ina Manchester.”
“To Daddy ALLAH ya kawoku lafiya, mizan dafa muku?”.
“Basai kin dafa komai ba ƴar Daddynta. Muda bazamu jimaba ma. Bye bye sai munzo”. Ya yanke wayar kafin tace wani abu. Bata damu ba ta zauna kusa da Smart da ke kallonta tana murmushi. “Mr A dama Daddy zasu zo shine baka sanar min ba?”.
Murmushi kawai yay mata baice komai ba. Itama sai ta dungure masa kai tana miƙewa. Fita tai a ɗakin zuwa kitchen ta barsa shi da ɗansa…..
★Tarba ta mutuntawa Daddy da Uncle Yousuf suka samu, shi Daddy wannan shine zuwansa na farko, Uncle Yousuf kam ɗan gida ne. Sun ci abinci a tare cikin farin ciki. AA na nane da Daddy dan akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakaninsu. Kasancewar ba wani jimawa akai da rabuwa ba bai manta kakan nasa ba. Bayan sunci sun sha sukai zaman abinda ya tarasu. Tsakanin Lulu da Daddy sun ɗan ƙara tattaunawa akan abinda ya faru tsakaninsa da Sulaiman da Mahaifiyarta. Yanzun ma sai da tai hawaye. Ashe babban kuka na gaba, dan lokacin da suka fara kallon abinda ke cikin camara ba Lulu ba hatta Smart da Uncle Yousuf sai da sukai hawaye. Daddy kam ƙasa kawai yay da kansa yana mai jin kewar matar tasa. Kuka sosai Lulu keyi na fitar hankali da ganin mahaifiyarta. Smart na son lallashinta yarasa yanda zai yi ga surukai. Dole ya hakura ya zuba mata ido sai tissue da yake faman miƙa mata na share hawaye, sai Daddy ne ya sakata a jikinsa ta gefe yana lallashinta. Yau jinta take kamar gata ga mahaifiyarta. Ashe dai haka suke tsananin kama, dan duk wanda ya ganta yasan mamanta yasan itace ta haifi abinta. Suna kama matuƙa tamkar tayi kaki ta ajiye ne. Ƙuruciya kawai Lulun zata fita. Ganin waɗan nan tsiyataku na Alh. Sulaiman ya sa Lulu cewa tanada shawara. Su duka idanu suka zuba mata alamar saurare. Zamanta ta gyara cikin dasashiyyar muryarta da kuka ya ɗasar ta ce,………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣8️⃣
…….“In dai muna son kama mutumin nan ya zama mai ƙarfin da bashi da mafita dolene sai mun haɗa hannu da Baba Garko, inba hakaba ko yazo hannu zai zama a banza ne, kai koda an kaisa kotu ne zai iya kuɓuta ma fa, idan ma an tsallake nan alƙali ya yanke masa hukunci to abokan huɗɗarsa zasu iya cireshi saboda yana huɗɗa ne da manya-manyan shegu na duniya bawai na Nigeria kawai ba. Duk da dai abu ɗaya dana sani ga manyan dilas na waɗan nan kayan a duk sanda sukaga zata kwaɓe musu ko zaka ci amanarsu zasu iya kashe juna. Ma’ana kamar yanda sukeyi akan duk wanda ya so bijire musu, shima ya koyo wannan ɗabi’ar ne a hannun turawan nan. Dan haka dolene zamuyi amfani da matakai uku na salon yaƙin kuma duk masu kamanceceniya da juna. Matakin farko shine Baba Garko, sai kuma kama duk wanda suke zagaye da Sulaiman ɗaya bayan ɗaya, hakan zaisa mu ruɗa masa hanjin ciki da jigata masa rayuwa mu sabautashi a tsaye. Hikimar saka Baba Garko anan itace yanada ƙarfi, sannan a fannin safarar miyagun kwayoyi shi maƙiyinsu ne, zai iya yin komai akan duk wanda hukuma ta cafke ta yanda bazasu taɓa kuɓuta ba. Mataki na biyu zamu ƙullama Sulaiman talala tsakaninsa da abokan huɗɗarsa musamman turawan nan na ƙasar Mexico. Kunsan duk wani shege akan harkar waɗan nan kayan yana ƙasar Mexico, saboda wannan matsalar na zagaye da rayuwarsu fiye da kowa a duniya, kuma nanne Sulaiman yafi safarar kayansa. Na uku dolene mu ɓoye kammu mu duka ta yanda idan muka kunnamasa wuta Daddy zai fara hara har zuwa wani mataki, saboda shi kaɗai yasan yana da camara ɗin nan, mu kuma zamuyi amfani da wannan fusatar tashi ne muyita fidda laifinsa waje ta yanda wasan zai zame masa gaba kura baya sayaki…”
Su duka babu wanda murmushi bai bayyana a kan fuskarsa ba, domin gamsuwa da shawaranta ɗari bisa ɗari. Albarka Daddy ya dinga saka mata, yayinda Uncle Yousuf ke tayashi. Smart dai na murmushi da binta da kallo ƙasa-ƙasa. Dan ya sake tabbatar da lallai matar tasa ƙwaruwace a lauyanci ashe tasan mutakeyi. Daddy ne yace, “Ni yanzu gaskiya bawani sanin kowa da kowa na cikin kasuwancin nayi ba, inma komai zai mana wahala sai dai wannan”.
“Shima bazai mana wahala ba Daddy, karka manta lungu da saƙo na sani, nasan manya da yara masu wannan business ɗin, kuma duk da haka zan nemo Nadiya itama, duk da bana jin zata bamu haɗin kai ta ciki sauƙi saboda abinda nai maita a last rabuwarmu, amma zan ƙoƙarta naga na ta dawo gareni saboda nasanta zata iya komai akan kuɗi, dan wannan ita ido ce a garemu tamkar google. A yanzu haka zan iya bada list na wanda wasan zai fara a kansu”.
Anan ma duk sun gamsu da zancenta, a take kuma ta zana musu sunaye da adireshin wajajen da take sayen kayayyakin, tun daga hannun ƙananan ƙwari har zuwa manya-manyan dila data sani a dalilin abokan huɗɗar nata. Ba kuma wai a wajen Kano kawai suke ba, a faɗin Nigeria gaba ɗaya harma da kasashen ƙetare dake maƙwaftaka da Najeriyar. Sosai Daddy yasha mamakin ganin waɗanda ta zano ɗin, har ma da Uncle Yousuf. Shi dai Smart ba kowa ya sani ba sai ɗaidaiku irin su Hon Nakowa suma dan sun kasance sanannun ƴan siyasa ne. Sai dai ganin sunan MM Atik Kumo ya sashi kallonta. Ta fahimci mi yake nufi, dan haka ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Shima Dila ne ai, ko’a ranar daka ɗakkoni a gidan nan tare da tsoffin nan gidansa ne, sannan shine ya sayar mana da kayan”.
“Shi wannan ɗin da nake gani simi-simi?”.
Lulu ta ce, “Humm bakaga komaiba ma, wasu ma dan ban san yanda zan misaltasu bane ku gane saboda sunan banza na sansu da shi, wasu kuma haɗuwar club ne kawai”.
Babu wanda ya sake iya magana dan sun san a zancen Lulun kam babu tantama…
A ranar su Daddy suka koma Manchester, dan washe gari suke son tafiya Nigeria su duka biyun, a Abuja kuma zasu sauka domin wucewa da su Twins, dan har Daddy ya nema musu transper zuwa Kano, duk da dai sun so bijirewa ya nuna musu basu isa ba. Har Mommy sai da ta kirashi akan hakan ya nuna mata babu ruwanta, ƴaƴansa ne, yanda yaso haka zai tafi da rayuwarsu. Dama dai da amincewarsa suke aiki a Abujar yanzu kuma yace su dawo gida suyi a gabansa. Jin ya buɗe mata wuta dole ta kama kanta, dan Daddy nada haƙuri, idan aka ƙuresa kuma akwai hayaƙi.
Tunda su Daddy suka wuce Lulu ta maida Camara ɗin nan abar kallo, sai da Smart ya ga kukan nata yayi yawa ya kwace ya ɓoye, duk roƙon datai masa akan ya bata ƙi yayi. Da ga ƙarshe ma ya ɗauketa suka fita. Wannan ɗan yawon da sukayi ne ya rage mata raɗaɗi da damuwar da take a ciki sosai. Dan basu dawo gidan ba sai da dare ya tsala kasancewar su daren da rana duk babu ruwansu bai hanasu hidimar gabansu. Washe gari ya kwasheta suka sake fita, sune har wajen gyaran jiki da wajen wasan yara aka kai AA duk da shi ba fahimtar komai yake ba. Wannan ɗan busy ɗin ya saka mata nutsuwa ta cire komai a ranta, sai sake duƙufa yima mahaifiyarki addu’a kuma.
Ahmad yay kiran Smart akan pharmacy da jami’an tsaro dana hukumar NDLEA sukaima dirar mikiya. Inda babu wani shan wahala aka gano na mahaifin aunty Khadijah ne dai, ta kai ma har an kamashi shi da yaran pharmacy ɗin gaba ɗaya. Duk da wasu sun rantse su basu san ana wannan baƙin kasuwancin ba. Sai dai ba’a sauraresu ba an ce sai abinda bincike ya tabbatar… Sosai Smart da Lulu suka tausayama Aunty Khadijah, dan Ahmad yace ana faɗa mata yanke jiki tai ta faɗi a asibiti, yanzu hakama tana can, bama ita kawai ba, zuri’ar gidansu gaba ɗaya suna cikin tashin hankalin al’amarin, dan abunne da babu wanda ya taɓa kawowa a ransa…..
*_NIGERIA_*
Tako ina komai a hargitse yake. Musamman ma a fanin iyalan Alhaji Sadi Dikkon da aka wayi gari da labaran kamashi, tare da yima babban pharmacy ɗin da sai yau mutane da yawa suka san nashi ne tsirara. Inda aka dinga nuna miyagun kwayoyin dake danƙare a cikin pharmacy ɗin da yanda ake kasuwancinsu a tsawon lokaci batare da hukumomi sun fargaba balle jama’ar gari da basu taɓa kawoma ransu ba. Gaba ɗaya Kano a rikice take da kace nace, saboda Alhaji Sadi babban mutum ne da ke a cikin jerin ƴan kasuwar da ake ji da su a Kanon dama ƙasar ta wani fannin. Sannan sam a fuska bazaka taɓa kawoma kanka zai iya aikata irin wannan ƙazamin kasuwancin ba.
Alh. Sulaiman na kwance a gidansa hankali kwance, yana ma tsaka da jin daɗin duniyarsa shi da amaryarsa kira ya shigo masa a waya kusan ƙarfe biyun dare. Rai a ɓace ya ɗaga duk da yaga Hon Nakowa ne a kan layi. Sai dai yana ɗagawar furucin Hon. Nakowa ya sashi zabura yana ture matar tasa gefe da lailayo wata gawurtacciyar ashariya mai kawuna goma sha biyu ya dire. Har neman taune halshensa yake wajen faɗin, “Tayaya hakan ya faru? Shi wane sakaci ne ya kaishi ga haka?”.
“Babu fa wanda yasan yanda akayi, Garko kaima kasan Alhaji Dikko na cikin mutane masu taka tsantsan matuƙa. Kawai dai akwai abinda ya kamata musani, sannan muna buƙatar zaman meeting na gaggawa dan nasan zuwa safiya zasu iya cewa zasu kamashi”.
“Wane zaman jira zai tsayayi ayi meeting da shi, a daren nan ya sayi ticket ya bar ƙasar nan kawai, idan kuma ya bari suka kamashi to tabbas zai mutu, dan mutuwarsa tafi rayuwarsa muhimmanci a garemu yanzu. Sauran aikin zamu ƙarasa a rufe zance. Dan haka kai kiran su Baita yanzun nan mu haɗu, dan muna buƙatar ganin shugaban NDLEA da IG ma kansa”.
Cikin gamsuwa Hon. Nakowa yace “Hakan yayi”.
Alh. Sulaiman na yanke waya idonsa ya sauka akan amaryarsa data zuba masa ido. Wani irin dafe kai yayi da faɗin, “Oh shiitt” dan harga ALLAH ruɗewa tasa ya manta bashi kaɗai bane a ɗakin ya zauna yana sakin zance har haka. A wani irin fusace ya nufeta, babu zato taji ya mata wata irin tsawa da nunata da yatsa. Har sai da ta zabura.
“Me kika ji?!!”.
Ya faɗa a gigice. Kanta ta shiga girgiza masa jikinta na rawa. “Banji komai ba wlhy Alhaji. Kwata-kwata banji komai ba”.
“Idan ma kin jin ki ɗauka baki ji ba, idan kuma kikace zaki nuna kinji kiyi kuka da kanki”. Da ga haka ya wuce fuuu zuwa toilet domin tsarkake jikinsa. Tashin hankali na haƙiƙa ta shiga, dan jikinta har rawa yake yi, zuciyarta kamar zata faso ƙirjinta ta fito. Gaba ɗaya kalaman mijin nata sun ɗimautata, so take tabar ɗakin ko zata samu iska, sai dai babu dama, dan fitar tata zai iya sawa ya zargi wani zataje ta faɗawa. Bata taɓa sanin atsabibancin mijin nasu ya kai haka ba, karo na farko a rayuwarta da taji ashe garama da ALLAH bai bata haihuwa a gidan nan ba..
Tana a kwancen ya fito, jikinsa duk laima bai damu ba ya saka jallabiya tare da zarar wayarsa da key ɗin mota ya fice. Da kallo kawai ta bishi kamar matacciya, dan ko dogon numfashi bata iyayi saboda tsabar tashin hankalin da take ciki..
★A lokacin da su Alh. Sulaiman ke nufar inda zasu haɗu meeting a lokacin jami’an tsaro sukai dirar mikiya gidan Alhaji Dikko dake ƙoƙarin sulalewa ya bar gidan batare da sanin ko iyalinsa ba. Aiko a take sukai ram da shi. Jiniyar motocin jami’an tsaron ne ya fargar da iyalinsa dama ƴan anguwa. Hankalin kowa a tashe, yaran sai kuka suke suna kiran yayunsu a wayoyi, ta hakane Aunty Khadijah da batasan mike faruwa ba tun safe da aka fara tone-tone a pharmacy ɗin mahaifin nata da ita kanta bata taɓa sanin nasa ɗin bane labari ya risketa daga bakin ƙaninta. A wajen ta yanke jiki ta faɗi tana tsaka da duba mara lafiya. Tun a daren Coach da Ahmad suka nufi asibitin cikin tashin hankali. Shine ma ya samu damar kiran Smart suka tattauna bayan aunty Khadijah ta farfaɗo an mata allurar barci mai ƙarfi. Zuwa safiya labari ya ƙara karaɗe ko’ina da ina, yayinda shugaban NDLEA na Kano dama na ƙasa gaba ɗaya suka ƙi ɗaga kiran su Alh. Sulaiman. Hakama IG da CP basu ɗaga musu kira ba. Abinda basu sani ba shine akwai wata ƙullaliya tsakanin gwamna da Alhaji Dikko, yana samun labarin abinda ke faruwa yay kiran CP da shugaban NDLEA na jiha yay musu gargaɗi. Tare da tabbatar musu in suka bari Alhaji Dikko ya ƙuɓuce musu a bakin aikinsu. Sannan Baba Garko ogan Gwamna ne na amana, dan haka yay kiranshi shima akan su IG da shugaban NDLEA na ƙasa. Shi baba Garko dama abune daya tsana a rayuwarsa, yake kuma yaƙi da masu alaƙa da shi, amma sam bai san akwai alaƙa tsakanin ɗansa Sulaiman da Alhaji Sadi Dikko ba sam…
Matuƙar tashin hankali sun shiga jin an cafke Alhaji Dikko, a take meeting ɗin su ya canja akala zuwa shirya yanda zasu kashe Alhaji Dikkon kawai. Dan sunci alwashin bazasu taɓa barinsa ya tona musu asiri ba. Sai dai dolene suyi komai ta ƙarƙashin ƙasa saboda gujema idon mutane a kansu. Sun nema amintattunsu dake cikin jami’an tsaron, kai tsaye suka basu umarnin kashe Alhaji Dikko ta hanyar guba. Kasancewar suma abokan cin mushen nasu ne sukai na’am da hakan. Dan in dai aiki ya buɗe suma nasu ya buɗe ai……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣9️⃣
…….Kowa da abinda ya damesa. Duk da abinda ke faruwa a jihar ta Kano ya girgiza Abba hankalinsa a rabe yake gida biyu a dalilin halin da Ummah ke ciki. Duk da ma dai malaman da aka kawo a wannan karon su sunyi jarumtar tsayawa, sai dai daga kallo ɗaya da sukai mata sukace ta koma cikin ɗaki kawai. Sun tattauna da Abba akan dolene asan mushurikin da yay mata wannan aiki. Cikin nuna rashin amincewa Abba yace shi babu ruwansa. Babu inda zaije neman wani akan aikin da bai aiketa yi ba. Babu irin lallashin da ba’ai masa ba yace babu gudu babu ja da baya. Da ga ƙarshe dole ƴaƴanta ne suka nufi wajen Hajiya Naqiba da ke gida, dan asibiti sun sallamesu kamar yanda suka buƙata akaje akai mata ɗorin gida. Sun sami Hajiya Naqiba a yanayin daya tada musu hankali, dan ƙafarta tai wani irin mahaukacin kumburin da har tafi gangar jikinta girma. Kuka take sosai da ihu na azabar zogi da raɗaɗin da ƙafar kemata. An kira mai ɗori ya tabbatar musu ta sake gocewa, ma’ana dai ɗori baiyi ba. Ya kuma tabbatar musu da shi gaskiya bai san yaya zai yi ba, sai dai su nema wani kuma ya gwada sa’arsa. Daga haka yay tafiyarsa ma shikam. To shine fa ƴaƴan Umma suka samu ana shawarar neman wani mai ɗorin dan an tabbatar musu na gargajiyar dai yafi kar su maidata asibiti. Ga mijinta ya nuna kamar ma abin bai damesa ba duk da irin kiran sunansa da take famanyi shi da ɗanta Maheer. Shi Maheer ɗin da farko ya zauna, da ga baya yay ficewarsa acewarsa shi gaskiya ihun da take ya ishesa, yana fita suka haɗe da abokansa sukai tafiyarsu wajen ƙwalewarsu da kayan shaye-shaye. Dole yaran Umma suka dawo gida jiki a sanyaye. Sun sake iske tashin hankali Umma dake wani irin nishi a ɗaki amma kowa ya kasa shiga ya dubata, Ammah ce ma ta nuna zatai ƙarfin hali Abba ya tabbatar mata idan ta shiga sai ya ɓata mata rai, dole ta kama kanta cikin damuwa. Suma ɗin dai babu wanda yay yinƙurin shigar saboda tsoro….
Har yamma babu wanda yasan halin da Ummah ke ciki, sai yayanta Jibirin ne ma yay ƙarfin halin bada shawarar a sake kiran malaman nan koda taimakon da zasu musu. Kowa ya bada goyon bayan hakan. Dan haka akai kiransu. Babu jimawa suka iso kasancewar akwai sanayayya tsakaninsu da Jibirin ɗin. Addu’oi sukayi da ƙarfin halin cusa kai a ɗakin, sai gasu suna rige-rigen dawowa a guje. Har yaran gidan dake tsakar gida na tayasu da afkawa ɗakunan iyayensu. Sun tabbatar da gaskiya bazasu iya ba, wannan mummunar halitta ganinta ai tashin hankaline ma. Sun tabbatar da shawararsu kawai ya kamata a bi aje a nemo mutumin da yay musu wannan aiki zaifi sauƙi fa. Wannan al’amari ya sake tayarma da kowa hankali. Dole ƴan uwanta suka tattaru neman mafita su da ƴaƴanta. Dan Abba dai da gaske ya juya musu baya…..
________★
Al’amari kamar wasa Dada sai da ta kwanta asibiti na kwana biyu, randa aka sallamonta ta samu surukanta cike da gida sunata harkokin arziƙi akan zaman bakwai. Wannan abu ya sake dugunzuma mata zuciya. Baba Garko ya shigo dubata da daddare ta sanya masa kuka. Kallonta kawai ya tsaya yanayi, bawai baya jin tausayinta bane, ba kuma baya sonta bane. Ya riga ya ɗaura ɗammarar horatane kawai. Dan ko auren nan nashi yayisa ne da gayya danya ƙona mata rai tunda yasan babu abinda ta tsana a duniya irin kishiya. Kuma ya samu nasara. A yanzun ma cikin ɓacin rai yaja tsaki da faɗin, “Ni al’amarinki kam ya fara bani tsoro Hajara. Shin wai baƙin ciki kike da ƙaruwar dana samu ko yayane? An faɗa miki haihuwa kin yanke jiki kin faɗi sumammiya, yanzu kin sakani a gaba kina kuka. Kin ganni nan ni bana son damuwa ina cikin farin ciki a ɓata min shi. Idan kinga zaki sakama ranki dangana ki saka, idan kuma kinga wannan halin da kike neman jefa kanki ne abin burgewa sai ki cigaba. Dan bakin alƙalami dai ya rigada ya bushe. Takardu sun jima da rubutuwa babu wata cleaner ɗin gogesu. In sha ALLAHU nan da wata shekarar ma wasu biyun zata sake zubomin a gidan nan, sai ki shirya sake suma. Na barki lafiya”. Da ga haka yay ficewarsa. Sama da ƙasa numfashin Dada ya ringayi, jininta yay masifar hawan da har idanunta na koma mata dishi-dishi, ALLAH ne ya taimaketa Uncle Muneer ya shigo ya sameta a lokacin, da tabbas zuciyarta zata iya bugawa komai ma ya faru….
(To Baba Garko ALLAH ya raya ƴan biyu. Koda yake kace nanda baɗi ma wasu kake so. Kaga tsoho da rigima🥱😂😂🤣🚴🚴)
*_★UK★_*
Alhmdllh a ɓangaren ango da amarya komai na tafiya dai-dai. Basu da wata damuwa sai cilin ɗinsu sukeyi. Duk abinda kuma ke faruwa a 9ja a cikin kunnensu yake. Dan suna samun information sosai ta hanyar Ahmad da su Daddy da suka koma gida. A yanzu haka tarko na biyu suke shirin ɗanawa. Dan sun gama shirya komai tsaff lokaci kawai suke jira.
Soyayya suke zubama juna mai tsayawa a rai da zuciya harma da gaɓɓan jiki. Duk da Lulu na dojewa da ɓoye nata sirrin har yanzu ta gagara furtawa a baki sai dai Smart ya gani a aikace. Dan zuwa yanzu kam karatun malamin nata tsaff ta haddacesa tama koma ruɗa masa tunani da salo-salonsa. A ranakun da yake da wasa koda ba’a cikin London bane bata iya zama, binsa take su tafi ga ɗan yaronsu da kowa ya gani sai ya tanka. Dan haka Smart ya dage da tofe abinsa da addu’a itama yana cemata tai masa saboda baki.
Lulu aja rigima bayan ta kira Baba Garko sun masa barka ita da Smart, ta kuma kira maijego da zuwa yanzu sun ƙulle sun zama ƙawaye dan kawai ta turama Dada haushi. Waya ta ɗaga tai kiran Dada. Bayan su. Gaisa Dada na zaton Lulun ta sakko ne daga fushin da take da ita zatai mata yaya jiki sai taji ta fara mata barkar haihuwar gidan. Dada ma bata san ta lailayo ashariya ta makawa Lulu ba. Aiko ta kwashe da dariyar ƙularwa tana mai yanke wayarta. Murmushi kawai Smart da ke zaune yana saurarenta yayi. Dan shi rashin jinta zuwa yanzu tsoro ma yake bashi wlhy. Baice mata komai ba sai da zasu kwanta ya mata faɗa. Tadai nuna masa taji, amma yasan batajin ba. Dan a ɓoye ta haɗa kayan jarirai na gani na faɗa ta bada aka wuce da su Nigeria wai a kaima maijego da jinjiraye….
Ana kwana na biyar da kama Alhaji Sadi Dikko Aunty Bilkisu da Iya tabawa suka iso Unitet Kingdom tare da Ahmad. A ranar Smart baya gida sunje buga wasa. Sai Lulu ce taje tarbarsu duk da Ahmad yasan gidan. Sosai aunty Bilkisu da duk take a tsorace ta samu nutsuwa da ganin Lulu, cikin farin ciki suka rungume juna. Hakama Iya Tabawa yau Lulu harda rungumeta, yayinda Ahmad ya caɓe yaronsa a hannu shima. Cab suka shiga har gida, dan Lulu bata driving anan kasancewar bata da lasisi. Sai Smart kawai. Daga Aunty Bilkisu har Iya Tabawa gidan ya birgesu sosai. Sunata santi da jera addu’a ga Smart. Abincin da Lulu ta shirya musu sukaci, bayan sunyi nak Ahmad yace zai wuce can ya samu Smart. Zuwa gobe sa dawo tare ɗan ba’a ranar Smart ɗin zai dawo ba. Tafiyar Ahamd ta sake basu damar ɓararrejewa, dan ma Aunty Bilkisu ba daɗin jikinta take ji ba sai ƙarfin hali kawai. Sun ɗan taɓa hira kafin Lulu ta kwashesu zuwa asibiti dan a yau take son aunty Bilkisu ma ta fara ganin likita. Kuma ko Smart baisan da hakan ba, dan shi nashi shirin kawai sai ya dawo ya kaita da kansa.
Kasancewar Usman da Dr Lameer ne suka haɗasu da likitan basu wani sha wahala ba na ganinta. A take aka bama aunty Bilkisu gado. Abinka da inda aka san darajar ɗan adam babu ɓata lokaci suka fara mata gwaje-gwaje da duk abinda ya dace. Koda Smart yay kiran Lulu bayan sun tashi a wasan bata sanar masa suna asibiti ba. Sun dai gaisa tai masa congratulations dan ganin sunci wasan suka ɗanyi hirarsu ta soyayya sukai sallama. Da yace ta haɗashi da su yay musu barka da zuwa Iya Tabawa kawai taba tace aunty Bilkisu na barci. Bai kawo komai a ransa ba ya yarda. Sallama sukai fan yana tare da Ahamd daya sameshi a can. Da ga haka itama ta cigaba da kai kawonta tare da Dr Lameer dake taimaka mata. Kasancewar mai jiyya ba zama yake a asibitin bayan ayi mata abubuwan da duk suka dace na wannan lokacin suka dawo gida, sai bayan wasu awoyi zasu koma dubata kuma……
*_★9ja★_*
A gidan Baba Garko suna akaci na kece raini da nunawa tsara. Dan ƴan biyu kam sunyi goshi matuƙa sannan sunzo da farin jini a wajen dangi. Kai da kaga taron nan kasan da gayya akayisa. Kasancewar su kansu dangin Baba Garkon ba daɗin Dada sukeji ba yasa a wannan gaɓar suke maida murtanin bashin gaba. Dan raƙashewa akai iya raƙashewa. Ga matan ƴaƴansa da jikoki cike taf da gida. Su kansu ƴaƴan dole sukazo kowa kuma da tsarabar suna. In ba haka ba kaci ubanka hannun mai gayya mai aiki. Alh. Sulaiman ne kawai babu, amma iyalinsa duk sun zo a sace batare da ya sani ba. Dan sukam dai basu yarda sun saka kansu a cikin faɗan iyaye da ɗansu ba. Hajiya Turai kuma tsaye take akan ƴaƴanta bata basu fuskar da zasu guji kakanin nasu ba. Tace babu ruwanta suma babu ruwansu. Ko Tajuddeen dake a cikin case ɗin tsundum cikin hikima ta dawo dashi ga kakaninsa tsundum. Dan tasan abinda take yi.
A yanda Dada ta koma laƙwas sai ta baka dariya ma da tausayi. Ba komai ya jawo hakan ba kuma sai kufcewar duk wata power nata. Gaba ɗaya ta fahimci komai fa ya gudu. Dan hatta matan ƴaƴan nata da take bama gwale-gwale yanzu kar suke kallonta. Bama sa shakkar dubar tsakkiyar idonta su yaɓa mata habaici a kaikaice. Karo na farko a rayuwarta datai kuka mai yawan gaske a dalilin tuna mahaifiyar Lulu. Tasha gaya mata gaskiya akan ta rage tsananin da takema matan ƴaƴan nata, in ba hakaba watarana sai sun nuna mata sun fita iyawa. Hakama dangin babansu ta daina musu wulaƙanci musamman marasa shi ɗin nan, kada wataran a auro wata a gidan ta riƙesu su rama duk cin kashin da take musu. Amma akoda yaushe saita hantareta harma da zagi saboda takaici da baƙin cikin ta kira mata kishiya, takance badan tana kama da Baba Garko ba itako da tace an mata misayarta a asibiti ne. Iya ƙoƙari Mawaddat tayi a kanta wajen gaya mata gaskiya akan abubuwa da yawa, yau gashi bata kusa da ita balle taji mata ciwon abinda ke faruwa. Dan ta kula ƴaƴa mazan nan fa ƴaƴansu da matansu kawai suka sani, tunda gashi kowa gani yake ta tsananta da kishin amaryar ubansu, ko kunyar faɗa mata hakan basa ji. Ko yau da safe Uncle Khamil da yazo sunan shi da nasa iyalin takanas da ga Abuja sai da yay mata irin wannan ƙorafin. Hakama autanta daya aiko da shatara ta arziƙi tun daga Saudiya. Gaba ɗaya saita fahimci goyon bayan mahaifinsu suke sam bata sonta ita yanzu. Babu abinda yafi ƙona mata rai da zuciya sama da saƙon Lulu, ita sai yanzu ma take sanin wai Lulu bata Nigeria tabi mijinta, bama wannan ba, shi kansa Smart ɗin bata san ya zama wani abu ba sai yanzu………✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣0️⃣
…….Haka dai ta yini a ɗaki tana ƙulla wasikar jakai, sai wanda yaga dama yake shigowa gaisheta da jiki. Kowa yana tsakar gida yana raƙashewarsa hankali kwance harda su DJ suka saka Dan taro akai fa na gani na faɗa a harabar gidan. Ga abinci da kuɗi ana bishasha kamar ba gobe. Babu wanda ya damu dawai cewar Dada nada hawan jini bari a sassauta. To kowa sha’aninsa yake kamar ya manta da ita a gidan, sai ƴayanta ne kan ɗan leƙata time to time. A ƙarshe dole sai da likita yazo dubata. Washe gari da Uncle Khamil zai wuce ya roƙi Baba Garko ya bari ya wuce da ita Abuja ta ɗan huta. Cayay shi babu ruwansa duk ma inda zata taje. Wannan kalma ta sake sanyaya musu jiki. Yayinda Dada ta ɓarke da kuka akan ita babu inda zataje, ba komai ta tuna ba sai wahalar da tasha a hannun matar Uncle Manner. Babu yanda basu lallaɓata ba tace wlhy babu inda zataje garama idan mutuwa ce ta ɗauketa a ɗakinta yafi mata. Dole suka barta suka wuce….
(Su Dadancy anji gwale-gwale 🤣🤣🚴)
_______★
Gaba ɗaya nutsuwa ta ƙauracema su Alh. Sulaiman. Dan sunbi duk matakan kawar da Alhaji Dikko al’amarin ya gagara. Duk wani babban ɗan siyasa da suke tare da shi a baya sun bisa amma kowa ya kife musu ciki akan case ɗin. Hakan ya sakasu fahimtar akwai wani babban ƙulli a ƙasa. Dan ko inda Alhaji Dikko ke ɓoye babu wanda ya sani a cikinsu har yanzu. Sun nema ganawa da gwamna amma hakan ya gagara, hasalima amsa ɗaya ake basu a koda yaushe shine yana Abuja. Tashin hankali na biyu a randa Alhaji Dikko ke cika kwanaki tara a hannun hukuma akai ram da babban yaron Hon. Nakowa. Da yamma sai ga labarin kama MM Atik Kumo shima. Kama MM Atik Kumo ya matuƙar ɗaukar hankalin jama’a fiye da na Alhaji Dikko saboda kowa yasan MM Atik Kumo dai ɗane ga tsohon gwamna M Atik Kumo, kuma ogane na gwamna maici a yanzu dan shine ma ya tallata shi ya kuma tsaida shi a takara. Wannan al’amari shiya ƙara maida hankalin mutane da yawa akan case ɗin, yayinda cecekuce ya ɓarke kasancewar kawunan jama’a na neman rabuwa. Wasu na ganin aikin gwamna na ƙyau, wasu na ganin al’amarin akwai lauje cikin naɗi dai. Sai dai yanda mahaifin MM Atik Kumo ya fito yay magana da nuna goyon bayansa akan aikin da gwamnan ya fara da kuma binsa da fatan alkairin kammalawa yasa zukata girgiza. Gwamna ya fara samun mafi rinjayen yabo ga mutane, suna ganin zuwa yanzu da gaske ake aiki za’ayi tuƙuru. Wasu kuma na ganin duk lumbu-lumbu ne kawai na ƴan siyasa musamman da ya kasance gab ake da yin zaɓe. Sai suke fassara abinda ke faruwar da kamar campaign ne kawai, komai na lafawa za’a saki duk wanda aka kaman.
To a baɗini zamu iya cewa kam harda hakan. Domin kuwa shugaban ƙasa shi abinda ke faruwa a Kanon yaja hankalinsa da ganin cewar in fa ya tallafa aka riƙe wannan makamin a ƙasar gaba ɗaya komawa kujerunsu babu fashi. Dan haka ya riƙe wuta shima tare da motsa sauran gwamnonin akan wannan aikinkin fa na kowa ne. Hankalin wasu a ciki ya tashi, kasancewar suma a cikinsu akwai ƴan safarar, wasu ma tsumu-tsumu suna cikin group ɗin na su Alh. Sulaiman ɗinne. Tuni suka fara kaima su Alh. Sulaiman labarin wannan fa al’amarin babba ne, dole akwai ta inda ake kunno wutar kuma dan shugaban ƙasa ma da kansa ya ɗauki lamarin da muhimmanci. Sun tabbatar da hakane kuwa a dalilin kame yaransu da aka cigaba dayi da customers ɗin su ƙananun diloli irin na anguwa da ƙauyuka. Gaba ɗaya duk sai suka sake susucewa da tunanin waye ke buɗe musu sirrika irin haka. A take fa aka fara zaman meeting meeting da bincike-bincike domin kamo bakin zaren. Duk wanda suke tunanin zasu iya buɗe musu aiki sun sakasu a faifai, Daddy shine na farko, dan haka suka zuba masa idanu. Sai dai me ta ko ina sun kasa gane komai, dan iya bibiyar Daddy da suka saka anayi babu wani motsi daga garesa a kansu. Hasalima wani business ya maidama hankali sosai. Al’amarin ya fara sakasu a ruɗani, suka cigaba da bibiyar duk wanda suke zargi amma basu gane komai ba. To dama hasashe ne kawai, domin sun tabbatar duk da wanda ke musu wannan illar ba ƙaramin sani yay musu ba. Sai kawai suka fara zargin junansu kuma. A randa sukai wani zaman da har ya jawo sa’insa a tsakaninsu suna barin wajen meeting ɗin aka cafke Hon. Baita. Al’amarin ya fara kaiwa intaha, dan lokacin da labari yazo ma Alh. Sulaiman harda cin tuntuɓe zai faɗi sai da yaronsa Malami ya tarosa. Hankali tashe ya shiga gida tamkar zai tashi sama. Yana shiga ciki kuma yaci karo da wani bala’in. To bala’i mana, dan ya samu kwali ne da aka nannaɗe da leda mai ƙyalƙyali kamar gift. Da farko bai maida hankalinsa akan abun ba sai da Hajiya Turai ke sanar masa ga saƙo nan ɗazun aka kawo wai a bashi. Kamar zai share sai kuma dai bayan ya gama bige-bigen wayoyinsa ya jawo abun ya hau farke ledar. Dan yanzu ya fahimci komai ma da zai iya zuwa musu ba abin yarda bane ba. Babu komai a ciki face envelopes guda biyu. Babba da ƙaramar. Babbar ya fara buɗewa, inda yaci karo da hotunansa har guda huɗu. Na farko shi da wasu mutanen kudu ne abokan huɗɗar kasuwancinsa suna tsakkiyar cinikayya, dan gabansu akwai cocaine har jaka uku a buɗe, sai jakkar kuɗi daloli a wata jakkar daban, a hannunsa na dama riƙe da ɗauri ɗaya na haggu riƙe da parcket na cocaine yana murmushin sa na basanci. Hoto na biyu tare yake da karuwarsa daga shi sai ƙaramin towel tana zaune a jikinsa itama da towel ɗin. Rawa jikinsa ya farayi, sai da ya wawwaiga falon ya sake tabbatar da shi kaɗaine dai sannan ya tafi hoto na uku. Tare da budurwar tasa ne dai suna shan cocaine a wani guri tamkar club. Da ƙarfi ya jimƙe hotunan cikin hannunsa illahirin jikinsa na wata irin tsuma, shin wanene da wannan aikin haka?. Zuciyarsa dake kumburowa take ayyana masa a hargitse. Tamkar wanda aka tsikara ya fisgi ƙaramar farar envelope ɗin itama ya buɗe. Takarda ce guntuwa a ciki mai ɗauke da gajeren rubutu, da words ɗin cikinta bazasu gaza 150 ba…
*_Da ace kasan ma’anar kalmar gidan rina da baka taɓoba, da ace kasan ma’anar fara takalo wasan da bazaka iya ƙara sawa ba da baka kalleni a matsayin birin wasanka ba. Abinda baka sani ba, ni idan na fara bana ajiyewa sai na kai ƙarshe. Haka nake kwanto nakeyi tamkar mage ta hango abin farautarta, saika gama sakankancewa dana ɓace sai na maka dirar mikiya. Wannan match ɗin sharar fage ne, na zahirin a tsakiyar filin da za’ayi yaƙin DUNIYA na uku zamu ƙarasa shi. Sai ka fara shirin saka sulken yaƙin, danni nawa sun jima a jikina. Ya rage naka neman bindiga, nokiliya, takubba, bomb, domin kare rayuwarka, dan kaima gab kake da bin sahun abokan naka zuwa jail……_*
*_AMM✍️_*
Wani irin gigitaccen ihu ya saki yana mai ɗaga Centre table ɗin falonsa ya wancalakar da shi gefe. “Wanene kai? Uban wanene kai? Dan uban wanene? Idan ka isa ka bayyana kanka mana. Nace ka bayyana kankaaaaa!!”.
🚴🚴🚴Da alama dai Tsule ya fara zarewa bari nayi nan🥱
___________★
A ɓangaren Umma wahala da azabar ciwo ya sata fara sambatu. Tana kwance a ɗaki hawan jini na neman kaita lahira. Bata iya fitowa ba’a iya shiga inda take. Cikin ƙarfin hali tazo ƙofar ɗaki daga ciki ta zube tana kuka da roƙon a kira mata malam na kan tudu ya warware wannan asiri, su taimaka mata dama sai da ya faɗa mata in har asirin bai kama wani acikin Smart ko matarsa ba zai iya dawowa kanta. Batayi zaton hakan zata kasance ba shiyyasa ta amince. Da farko babu wanda ya fahimci abinda take nufi, sai da ta cigaba da kururuwa da ihu mutan gidan suka fara maida hankali a kanta. Aunty Amarya ce tai kiran Ammah dake ɗaki tana waya da Lulu. Duk da Ammah ta jima da wannan zargin a ranta zantukan Umma sun kiɗimata, amma baiwar ALLAH haka tai kiran Abba tana roƙonsa ya dazo gida. Kamar zaiƙi sai kuma dai yace gashi nan dama ba nisa yayi da gidan ba. Koda yazo yaji shima abinda Ummahn ke faɗi sai ransa ya sake ɓaci, wajen yay niyyar bari da tabbatar musu da shi fa babu ruwansa su kira ƴaƴanta. Sai da Ammah taita roƙonsa da magiya yaran gidan na tayashi sannan dai ya haƙura ya dakata amma yay kiran Yayanta Jibirin. Zuwansa yasa suka fara mata tambaya, da ƙyar take amsawa da basu adireshin inda malam na kan tudu yake. Anan ma Abba ya bijire bazashi ba, da ƙyar aka taru a kansa daban haƙuri dai, sai dai yace ba ranar ba dan bazaiyi tafiya cikin jeji da yamma ba. Dole suka barsa sai a washe gari aka shirya tafiyar a motar Salim da ya yarda zaije da ƙyar, dan shima sai ƙunƙuni yake akan tafiyar, damma dai Abba ba kanwar lasa bane.
Su biyar sukai tafiyar, Abba, Salim, Kawu Jibirin da Kawu Idi shima ƙanin Ummah ɗinne, sai ƙanwar Hajiya Naqiba da suka taɓa zuwa wajen da ita, itama wai zata amsowa ƴar uwarta magani dan ƙafar Hajiya Naqiba ta rure tana jan ruwa ne. Sun sha wahala, yayinda motar Salim taci ubanta a hanyar jejin cikin sahara, da ga ƙarshe ma dole suka ajiyeta a wani waje suka cigaba da tafiya da ƙafa. Matuƙar mamaki ya kamasu da ganin inda wai su Ummah ke zuwa yin mugun abu, can wani ƙauyen Jigawa ne, bama cikin ƙauyen bane a bayan gari bokan yake sosai cikin tsakkiyar sahara a saman dutse (dan bama ce malami ba). Duk azabar zafi ranar wajen baya damunsa, dan ko bishiyoyin kirki babu saboda sahara. Da ƙyar suka iya hawa dutsin, Salim ya fasa hannu, cikin zafin azaba da ɓacin rai ya ce,…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣1️⃣
…….. “Gaskiya Umma kin cucemu, haka kawai kin saka mutane zuwa wannan azababben wajen”. Babu dai wanda ya tanka masa a cikinsu. Wani yabiɗaɗɗen tsoho suka samu a saman dutsen jikin bukkarsa. Surutai yake tayi kamar wani zararre, yana ganinsu ya kwashe da dariya. Turus sukai duk suna kallonsa, sai ƙanwar Hajiya Naqiba da tasan haka yake ne ta zube tana masa kirarin da suke masa. Hakan ya sashi yin shiru yana saurarenta, sai da ta kammala ya sake kwashewa da dariya yana ma kansa kirari shima. Sai kuma ya tsuke fuska yana kallon su Abba kamar bashi yay dariyar ba, “To asararru, ku bazaku zube ku kwashi gaisuwar bane wajen waliyyin ALLAH?”.
“Waliyyin shaiɗan dai. Ubanka ne zai gaisheka matsiyaci haihuwar asara” Salim da hanunsa ke masa azaba ya faɗa a fusace. Kaɗan ya rage Kawu Idi yay dariya ya dai daure. Kawu Jibirin ne ya ɗan girgiza kansa da fuskantar boka na kan dutse. Babu wasa a tattare da shi ya ce, “Muba neman wani abu mukazo wajenka ba. Hasalima baka da wata daraja a idanunmu face kasancewa a gafalalle abin ƙyama”. Ya zaro wayarsa yana nuna masa hoton Ummah, wannan matar tazo wajenka kayi mata aiki akan wasu mata da miji, tare da tabbatar mata asirin idan baici ɗaya a cikin ma’auratan ba zai iya komawa kanta anyi haka?”.
Dariya nakan tufu ya kwashe da shi harda ƙyakykyewa. Sai da yay mai isarsa kafin ya tsagaita da faɗin, “Shegiyar kaya ai wannan tasan takan mugunta. Dan koni uban gayyar da kaɗan na ɗarata. Sai dai a yanzu haka tana can cikin bala’i hhhhh. Dama mun faɗa mata ƙaiƙayi zai koma kan masheƙiya bata yarda ba hhhhh. Asirin bai kama mijin ba matar kawai ya kama, itama kuma ya saketa hhhh. Dan haka ya dawo kanta kuma bazata taɓa warkewa ba hegiya ta shiga kamun ɗan ƙallau.”
“Kaima yau zaka shiga kamun ALLAH ai matsiyaci. Ka tsufa har an yayyafa maka gishirin mutuwa a saman kai amma baka san Annabi ya faku ba” Salim ya faɗa yana ɗaukesa da mari. Kafin kace mi ya rufesa da duka. Da ƙyar su Kawu Idi suka riƙesa, zafin dutsen dana ranar yasa suka yayibosa zuwa ƙasa bayan Kawu Idi da Salim sun ɗaureshi. Abba dai ko sau ɗaya baice tak ba. Haka suka jefashi a mota duk da warin jikinsa ma ya ishesu suka ɗauki hanyar Kano. Da yamma liss suka iso, sun sami gida jigum-jigum baka jin komai sai nishin Ummah. Ganin boka na saman tudu ya firgita mutane da yawa. Duk da shi a cewarsa ba boka bane malami ne, dan hatta shigarsa dai ta malam ce sai dai dauɗa da warin rana ba’a magana. Ga Salim ya tunɓuke rawanin tun a can sai ƙwalelen kansa da yasha ƙwal a kwabo…..
__________★
A bisa umarnin Lulu Ummita ta shiga binciken gidan su Nadiya ta hanyar yaranta na shagon saloon da yanzu ƙanwarta ke riƙe da shi. Da farko yaran nata sunji tsoro sunƙi faɗa saboda gargaɗin da akai musu. Sai da Ummita ta dinga musu magiya sannan suka faɗa mata gaskiyar a inda Nadiya take yanzu haka. Acan cikin wata tsohuwar makaranta ce da rufunta ya kwaye a ruwan bana. Hankalin Ummita ya tashi matuƙa da ganin Nadiya duk da bata santa ba kafin yanzu, sai hotonta data gani a wajen Lulu. Tayi baƙi ta lalace sai uban ciki haihuwa yau ko gobe. Wasu ƴan shaye-shaye dake zama wajen ke bata abinci da kayan shaye-shayen. Hankali tashe Ummita ta kira Lulu a video call. Da farko Lulu cewa tai bata yarda Nadia bace, sai da ta fashe mata da kuka cikin ƙarfin hali ta rantse mata cewa itace. Gaba ɗaya sai Lulu ta sake birkicewa da tashi hankali, itama ta fashe da kuka. Da ƙyar ta iya cewa Ummita sukai Nadia asibiti, amma ta kira Uncle Yousuf a waya. Koda Ummita tai kiran Uncle Yousuf ta sanar masa babu ɓata lokaci ya iso wajen shi da ƴan sanda da ambulance. An ɗauki Nadiya zuwa SHIRA’S HOSPITAL. Babu ɓata lokaci likitoci suka rufu a kanta, kamar jira cikin nata keyi dama sai naƙuda ta tashi. Doctors sun tabbatar bazata iya haihuwa da kanta ba, dole akai mata cs. Ana shiga da ita ɗakin theatre Uncle Yousuf ya nema gidan iyayenta. Sai dai koda yaje babu wanda ya sauraresa duk da ya sanar musu tana can a asibiti an shiga da ita theatre basu saurarensa ba. Haka ya baro gidan ransa a ɓace, sai bayan tahowarsa ƙanwarta ta biyosa asibitin a sace bisa umarnin mahaifiyarsu……
(ALLAH sarki Uwa kenan😭🙏).
*_★UK★_*
Fuskarsa ɗauke da murmushin zancen Iya Tabawa ya tura ƙofar bedroom ɗin a hankali ya shiga bakinsa ɗauke da sallama, zuciyarsa cike da ɗokin san ganin sahibar ruhin nasa.. Cak kalaman bakinsa suka tsaya sakamakon tozali da ita zaune fuska share-share da hawaye ta zubama waya idanu…
“Mawaddatan-warahmah!”.
Ya kirayi sunanta cikin wani irin salon taushin murya mai amo da ratsa zuciyar mai saurare. A bazata ta ji saukar muryar tasa duk da a tsumayen isowar tasa suke. Dan hatta kwalliyar da taci yau a cikin skert da riga na atamfa da sukai mata ƙyau tayine da shi. Harda kwalliyar da hawayen tausayin Nadiya suka gama batawa. A hankali ta ɗago idanunta da suka kaɗa harda ɗan kumburowa. Sai ya samu kansa da lumshe nasa da sake buɗe su a kanta ya ware mata hannayensa alamar tazo garesa. Babu musu ta taso da ɗan gudu-gudu ta shige jikin nasa ya maida hannayensa ya naɗe a nata jikin. Wani kukan da ya sakashi runtse idanu da ƙarfi ta sake saki tare da ƙara ƙanƙamesa. Komai baice mata ba, bai kuma hanata tayi kukan ba har tsawon mintina biyu. Sai da ya tabbatar tayi ya wadaceta sannan ya ɗagata cak zuwa saman gado. Kwantar da ita yayi tare da kishingiɗa a gefenta ya tokare hannunsa da tallafo kansa ta yanda zai iya mata runfa. Ɗayan hannun kuma ya tallafo fuskarta ya zuba mata ido. Itama kallonsa take tana jan ajiyar zuciya. Karo na farko ya sakar mata murmushi mai sanyi da saka babban yatsansa ya ɗauke mata hawayen.
“Waya taɓa Final Choice ɗin Aliyu Mawashi? Maman Aliyu Mawashi? Kin san kuwa yanda nake jin ƙunar zuciya a duk sanda naga hawaye na sauka akan ƙyaƙyƙyawar fuskar nan taki. A gaɓa ɗaya kawai nake son naga waɗan nan hawayen da rakinki, amma ba’a banza haka ba okay”.
Hawayen ne suka sake ciko mata idanu, a hankali ya shiga girgiza mata kansa alamar kar tayi. Haɗiyesu ta shiga ƙoƙarin yi, sai kuma ta juya ta sake rungumeshi. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da ɗago fuskarta ya manna mata kiss a goshinta da hancinta ya sakko saman lips ɗinta. “In sha?”. Ya faɗa cikin raɗa yana nuna mata lips ɗinta da yatsa. Murmushi ta sakar masa a karo na farko da hawaye. Shima sai ya murmusa da kai nasa lips ɗin saman nata. A hankali suka lumshe idanu a tare kowanne na sauke ajiyar zuciya, daga haka tsarin ya canja zuwa wani fage daban…
Yana zaune a bakin gado yana goge jikinsa da ƙaramin towel ta fito itama sanye cikin bathrobe. Idanu ya zuba mata cike da jin ƙarin ƙaunarta da tausayi, suna haɗa ido ta ɗauke nata cikin jin nauyi. Wucesa tai niyyar yi ya riƙo mata hannu. Batare data juyo ba ta furta, “Zan shirya ne fa na haɗa maka abinci”. Murmushi yayi da jawota baya ya zaunar a saman jikinsa. Cikin kunneta ya raɗa mata maganar da ta sakata jin rikicewa dan kunya, shiko ya shiga darawa abinsa. Tashi tai zumbur a jikinsa ta gudu zuwa gaban mirror tana murmushi da faɗin, “Ni dai babu ruwana wlhy”.
“Daga baya kenan yarinya”. Ya bata amsa yana tasowa zuwa gaban mirror ɗin shima. Da jikin mirror ɗin ya jingina, hakan ya basu damar facing juna. “Miya sakaki kuka?” ya jeho mata tambaya dai-dai tana ƙoƙarin warware gashinta data naɗe a cikin ƙaramin towel. Numfashi ta ɗan firzar a hankali idanun nata na sake cikowa da hawaye, murya a raunane ta ce, “Nadiya ce”.
“Nadiya kuma? Who is she?”.
“Ƙawata ce, sai dai bama tare yanzun”.
“Ya akai banji sunanta a labarinki ba?”.
“A Nigeria na santa ai, kaima kuma ka santa ma. Dan ka taɓa kai ni shagonta saloon”.
Cikin ɗan yin jimm na alamar tunani ya ce, “Okay na gane, ba itace kikace zata taimakemu ba?”.
“Yes ita”.
“Uhmum miya faru da ita?”.
Wayarta ta ɗauka ta miƙa masa. Amsa yay ya duba. Recording ne na video call da sukayi ita da Nadiya. Shi kansa da farko bai ganeta ba. Al’amarin ya girgiza shi da bashi tsoro. Jiki a sanyaye ya miƙa mata wayar batare da ya iya furta komai ba. A bazata Lulu data sake fashewa da kuka ta ce, “Aliyu nagode da ƙoƙarin ka a kaina, bani da abinda zan iya biyanka da shi a duniyar nan face na dawwama ina maka addu’a har ƙarshen numfashi na kai da Uncle Yousuf. Yanzu nima da ALLAH bai taimakeni, kun tallafi rayuwata kun cireni da ga wannan mummunar ƙazamar rayuwar ba da hakance zata kasance da ni. Abinda nake sha ko rabinsa Nadiya bata iya sha fa. Amma kaga yanda rayuwarta ta koma, bata da maraba da mahaukatan kan layi masu wucewa yara na musu atire. Iyayenta sun korota a makaranta data lalace take kwana tsakkiyar kazaman ƴan shaye-shaye. Na shiga uku Hydar wace irin rayuwa ce muke jefa kammu ne haka?….”
Hankalinsa ne ya ƙara tashi ganin yanda take kuka na fitar hayyaci. Ɗagota yay ya rungumeta a jikinsa, tare da fara jera mata kalaman lallashi da nasiha. Sun jima a wajen tsaye ya karasa busar mata da kan nata ya ɗaure mata shi. Cikin son kauda mata yanayin ɓacin ran nata ya ce, “Ina auntyn taki wai, naga da Iya Tabawa kawai muka gaisa tana goye da AA”.
Murmushi ta ɗan saki kaɗan, sai kuma ta kallesa tana ɗan lullumshe ido cike da salon dake narkar da mutumin nata tace, “Tana asibiti ai, tun randa suka zo”.
Da mamaki sosai a fuskarsa ya ce, “Asibiti kuma Madam”.
Sai da ta ɗan hararesa saboda kiranta Madam sannan ta bashi amsa. “Eh ai abinda ya kamata ayi kenan, mizai sa na riƙeta a gida har sai ka dawo kuma. Yanzu kam kaga har sun bamu ranar da zasu mata aikin ma. Sai ka ƙarasa shiryawa muje ka ganta dama Doctor ɗin ta buƙaci ganin mijinta, sai dai nace mata baya kusa sai ƙaninta dai.”
Rasama mizaice mata yayi shi kam, sai kawai ya zuba mata idanu yana kallonta, yana jin tamkar ya haɗiyeta ya huta ma kawai. “Kallon fa?”. Ta faɗa tana wani tura masa baki da kashe masa ido ɗaya. Hannu ya kai zai cafkota ta zille tana dariya. Shima sai ya murmusa yana dimtse gefen lip ɗinsa da haƙori. Kayanta ta maida dan bata son Iya Tabawa ta zargi komai tunda ta ganta da su. Ta dawo gaban mirror ɗin ta maida ɗaurin ɗan kwalinta kamar yanda yake ɗazun da yin ƴar kwalliya.
Shima sai ya nufi closed ɗinsa ya saka kaya. Tsaff suka fito suna zuba ƙamshi da annuri, ita sai yanzu ma ta san ashe tare yake da Ahmad. Amma yake komansa hankali kwance a ciki kamar bai bar kowa na jiransa ba, shiyyasa da zata fito ya sakata sanya abaya ashe. Sun gaisa da Ahmad yana faman tsokanarta kamar yanda ya saba. Ita dai nata murmushi ne musamman daya kasance boss ɗin nata ya watso mata kallon gargaɗi. Abincin da suka sha wahalar yi ita da Iya Tabawa ta gabatar musu. Sosai Smart yaji daɗin ganin tuwo, dan zai iya cewa tunda ya baro Nigeria bai sake ci ba. Kasa haƙuri yayi ya tambayi inda suka samo garin tuwo haka. Lulu ta bashi amsa da cewar su Aunty Bilkisu ne sukazo musu da shi. Bayan sunci sun ƙoshi kaɗan suka huta Lulu ta takura musu dole suka fice zuwa asibiti duba aunty Bilkisu, zuwa lokacin AA ya tashi yana hannun Babansa da yay kewa…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣2️⃣
……Sosai Smart ya tsinta kansa cikin farin cikin ganin ƴar uwarsa, duk da tana kwance a gadon asibiti hakan bai hanasu yin hira ba. Anan ne take basu labarin halin da Ummah ke ciki a yanzu. Babu ɗigon tausayinta a zukatansu sai Smart kawai, duk da yana jin ɗacin rabashi da matarsa da tayi hakan bai hanashi jin tausayinta ba. Dan ko babu komai tunda ya taso kallon uwa yake mata, sannan jininsa ce ita tunda ƴar uwar Abba ce. Sun jima a asibitin, dan Smart ya gana da doctor sun tattauna, daya buƙaci yanda biyan kuɗi zai kasance sai ya samu Lulu ta biya komai har kuɗin aiki dana gaba ɗaya zaman da zatayi ma a asibitin. Kasa cewa komai yayi har suka dawo gida. Sai dai sun sauke Ahmad a masauki. A falo suka sake zubewa aka ɗaura hira, Iya Tabawa na basu labari suna kwasar dariya. Sun jima a wajen kiran wayar Smart da akayi ne ya sashi miƙewa ya shige bedroom, hakan ya bama Lulu damar bin bayansa bayan wani lokaci. Ta samesa har lokacin yana waya da Usman da ke bashi labarin irin halin ruɗanin da Alh. Sulaiman da abokan cin mushensa suke a ciki. Sai saƙon daya bada aka aika masa ɗin nan. Sosai Smart ke kwasar dariya har yana jin inama yana Nigeria yaga wannan ruɗani a fuskar Alh. Sulaiman. Sai dai babu komai yasan zai gani ta cikin direct camara ɗin da suka sanyama Alh. Sulaiman batare daya sani ba. Bayan sun gama wayar ne yake bama Lulu labari, itama dai dariyar tasha da jin inama tana 9ja ake wannan irin cakwakiya haka.
AA ya tambayeta ta ce ai ya koma kwana wajen Iya Tabawa. Da mamaki yace, “Abincinsa fa?”.
“Wane abinci kuma bayan wanda yake ci ya ƙoshi. Ai ni na yayesa”.
“Yaye a wata goma sha ɗaya? Wane irin rashin tausayine haka Baby luv”.
“Haba kai kam miye abin rashin tausayi anan. Nifa wlhy dama so nake ya taka kawai, yaron da dama ba wani ya damu da shan nonon bane ba.”
“Kin dai so yayesa saboda kina buƙatar wani babyn”.
“Kamar ya?”.
“Kamar yanda kika ji mana”.
Ganin kamar cikin ɗan zafi yay mata maganar ya sata jan bakinta tai shiru. Ita matsalarta da shi kenan saurin fushi. Abu kaɗan bazai fahimcesa ba sai ya hau kamar fulawar burodi, sai idan shi yaso shanyewa ya nuna kamar bai gani ba. Bata yarda ta sake magana ba. Shima sabgar gabansa ya cigaba da yi batare da ya kulata ba. Ganin abin nasa babbane ta fita ta bar masa ɗakin dan bata buƙatar wani ɓacin rai kuma a yanzu….
Bayan kwana biyu da dawowarsa akaima Aunty Bilkisu aiki. Duk halin da ake ciki jama’ar gida sun san komai. Dan haka kowa nata faman addu’ar nasara. Alhamdullah anci nasarar kuwa, dan anyi aiki har an kaita ɗakin hutu, basu sami ganinta a wannan ranar ba sai washe gari da safe. Sunji farin cikin samunta a cikin hayyacinta. A take kowa farin cikin sa ya gagara ɓoyuwa. Fatansu kuma yanzu ALLAH ya bata lafiya. Smart bai sake ma Lulu magana akan yaye AA ba, itama bata sake tayar masa da zancen ba har ya sake barin London ɗin a weekend daya zagayo. Sunje yin wasa, yayinda ita kuma take cigaba da zama tsaye akan al’amarin aunty Bilkisu daketa samun lafiya. Kullum sai sunyi waya dasu Ammah da kuma ƴan gidansu ta video call, musamman ma Ummita da ke tsaye akan al’amarin Nadiya dake a asibiti ita da Uncle Yousuf. Kwanan Smart uku ya dawo, yayinda Ahmad ke shirin komawa Nigeria. Taka tsantsan ta dingayi a ƴan kwanakin nan na ganin saɓani bai shiga tsakaninta da mijinta ba. Alhamdullah kuwa anci nasara, dan banda murzar juna babu abinda sukeyi sai zuwa asibiti wajen aunty Bilkisu da ɗan fita hutawa domin bama kansu farin ciki. Sosai kuma suna samu, dan yanda suka murje tsaff da su, ga tattalin juna da nuna kulawa kowa yasan hankalinsu ya kwanta. Sun kuma samu nutsuwa irin wadda duk wani mai aure ke buƙata a rayuwa. Sai ɗan saɓanin da ba za’a rasa ba na tsakanin harshe da haƙori dake zuwa yau da gobe. Duk yanda Lulu zatayi kuma takanyi na ganin abin baiyi nisa ba ta shawo kan abinta ya huce, shima kuma da yake bason ganinta a damuwa yake ki ɓacin rai ba baya barin abin yay nisa sam…..
*_NIGERIA_*
Alhamdullah an samu nasarar dawowar Ummah dai-dai, nakan dutse ya gama kunce ƙullin daya ƙulla su Salim suka miƙashi hannun ƴan sanda batare da sun saurari bayanin da yake musu akan bafa wai Ummah ta kuɓuta bane ba ɗari bisa ɗari, dolene sauran bala’oin data saka akai mata aiki akan Smart ɗaya bayan ɗaya zasu cigaba da dawo kanta. Sai ta shirya. Babu wanda ya sauraresa, sai yan jarida da suka kafa suka tsare har sai da suka samu cikakken bayani a bakinsa. A take fa al’amarin Umma ya shiga media da duniyar yanar gizo dana kafafen ƴaɗa labarai musamman irin na rediyo. Kafin kace mi mutane da yawa sunji kuma sun sani anata ALLAH wadai da al’amarin nata tare da mata irinta.
Ana wucewa da nakan dutse dole itama Ummahn aka kwasheta zuwa asibiti dan hawan jini ya mata biji-biji. A asibitin ma dai ƴan jarida basu barsu sun huta ba da jama’ar gari ƴan so da jin ƙwaƙwaƙwaf. Musamman ma da ya zam hotunan Ummah sun gama zagaye gari a suffar Dodo, saboda lokacin da nakan dutse ke ƙoƙarin warware asirin mutanen da suka samu shigowa musam yaran maƙwafta ɗauka suka dinga yi a wayoyi suna sakawa a shafukan su na sada zumunta. Dan danan fa sunan Ummah da Hajiya Naqiba yay amsa kuwwa a duniyar labarai da yanar gizo. Dan hatta Hajiya Naqiba basu bari ba sai da suka bibiyi al’amarinta.
(Su Umma an zama celeb…. sai ku tayata murna🤣😂).
A washe garin da aka wuce da Umma asibiti Smart ya buƙaci su koma gidan daya kama musu domin fara gyara wanda suke a ciki. Kusan dama a shirye suke da hakan, dan haka babu ɓata lokaci suka tattara zuwa can ɗin nan kuma aka bajeshi aka fara aiki bisa tsayawar Coach da manyan yaran gidan duk da Salim ya nuna hassadarsa a fili. (Nonon Ummah ba wasa ba ai🤣🙏).
Suko su Mubarak farin ciki suke abinsu ganin za’a gyara musu gida. Sai addu’a da fatan alkairi suke jerama Smart. Mazansu da matansu haka suka dinga kiransa suna godiya. Duk da wasu sun gagara hakan musamman a mazan saboda baƙin ciki. Dan Mama ita kanta a wannan gaɓar Hassadarta ta gagara ɓuya. Sai da taga Abba na neman birkice mata ne fa ta kama kanta. Sai ƴaƴanta mata da suka nuna mata karfa ta tafka kuskure makamancin na Ummah. Dole ta kama kanta ta koma yaƙe da addu’a a fatar baki. Ƙasan zuciyarta kam kamar zata ƙone, a ganinsu dai ƴaƴansu ne sukafi cancanta da wannan arziƙin.
Ni dai nace, “Hummm🥱🚴🚴”.
__________★
A ɓangaren su Alh. Sulaiman suna tsaka da kukan targaɗe sai ga karaya ta samu. Dan kuwa dai al’amarin Nadiya ma ya bayyana wa duniya. Inda ta tabbatar da cikin jikinta na su Hon. Nakowa ne dan su duka babu da wanda bata mu’amula. Ta kuma tabbatar da cewar su ɗin manyan diloli ne na miyagun kwayoyi, dan ko ita sune suka koya mata shaye-shaye. Ta kuma tabbatar da in har sunce ƙarya ne su fito duniya su musa zancenta ita kuma zata bada manyan hujjoji a kansu. Tace bayan itama akwai yara da yawa da suka lalatama rayuwa ta hanyoyin shaye-shaye da zinace-zinace. Wasu sun jima da rasa ransu, wasu iyayensu sun koresu a gida sun shiga duniya. Wasu kuwa a gidan iyayen nasu ake lalata musu rayuwa batare da iyayen ma sun sani ba. Acewarta Bama su kawai ba, akwai manyan ƙasar da dayawa sukai suna da nisa a irin waɗan nan al’amuran, su suyi ƴaƴansu suyi. Ba kunya Uba da ɗa za’a haɗu a club ko da ƴa anama juna kallon kallo. Akwai wanda ake kaima yara ƙanana gida suyi musu fyaɗe, wasu ma harda maza sukemawa. Ta tabbatar da idan zata tona asirin mutane da yawa akan wannan al’amarin tofa manyan nan da yawansu bazasu sha ba a bisa madafun ikon da suke kai. Dan haka a rufe rufau kawai. Wannan video ya girgiza al’umma da yawa. Yayinda ya bama wasu da ke fuskantar irin raɗaɗin da Nadiya ke a ciki fitowa suma suyi magana. Fiye da yanda ba’a zato al’amari ya sake rincaɓewa. Dan kuwa a ranar kame na hauka jami’an tsaro sukayi, kuma duk yaran su Alh. Sulaiman ɗinne da Nadiya ta dinga lissafowa a faifai. Inda kuma duk akayi dacen kamasu dumu-dumu da abinda ta lissafa ɗin kasancewar dama sai da aka shirya musu talala aka saki video ɗin.
Zuwa yanzu kam su Alh. Sulaiman sun tabbatar da akwai mai musu zagon ƙasar nan. Duk da shi zai iya bugar ƙirji akan babu ruwansa da wata yarinya a cikin garin kwano. Iskancinsa a wajen Nigeria yakeyi sai ko Lagos. Dan budurwarsa ɗaya ce tak a Nigeria kuma a Lagos take zaune. Asalinta ma ba ƴar 9ja ɗin bace shine ya kawota ya ajiye. Sai dai kalmar fyaɗe da akace akwai masu yima yara kam ya girgiza shi, dan abune da anan kam baida tacewa. Dan haka idanunsa suka fara rufewa ya dannama Daddy kira dan ya fara ji a ransa anya Daddyn baida wata rawa da yake takawa a al’amarin nan kuwa. Duk da a yanzu haka ana tsaka da masa bincike akan *_AMM_* ɗin nan da ya aiko masa da takarda da hotuna, har yanzu kuma ya kasa hasaso kowa, ba komai ya jawo haka ba kuma sai kansa dake a birkice…..
★★ Daddy na a gidansa hankali kwance dan kallon wasan su Smart ma yake tare da su twins. Da farko kamar bazai duba mai ma kiran nasa ba sai kuma dai ya ɗauki wayar. Yasha mamakin ganin Alh. Sulaiman Garko. Har ya maida wayar ya ajiye da nufin sharesa sai kuma dai ya ɗaga tare da miƙewa ya shige bedroom ɗinsa.
Cikin wata irin gigitacciyar tsawa Alh. Sulaiman ya ce, “Isma’il mai kake tunanin ka taka ne?!”.
Daddy ya saki murmushi mai sautin da har Alh. Sulaiman na jiyosa. Kansa tsaye babu alamar ɗar a tattare da shi ya amsa masa da faɗin,…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣3️⃣
…….“Banda abinka Sulaiman Garko idan kaji makaho yace ai wasan jifa ai ya taka dutse ne. Toni a wannan gaɓar dutsina na taka bama dutse ɗaya ba. Sorry fa, inata son zuwa na maka jajen abubuwan dake ta faruwa amma nayi busy da yawa. Sai kuma naji yau ma wata yarinya ta ɓaro muku babban aiki, dan kaima banace bakayi ba. Wanda zai iya yima ƙanwarsa uwa ɗaya uba ɗaya fyaɗe ai abune mai sauƙi yayma sauran ƴaƴan jama’a ciki harda wanda ya haifa ma…..”
“Da hannunka kenan a ciki? Dama an tabbatar min da yarinyar ƙawar ƴarka ce ai. Isma’il karka manta ni zaki ne. Nakanyi farauta a duk dajin da yay min na kuma ci kowacce irin dabba na zauna lafiya batare da ko jin ɗar ba tattare da ni….”
“Banda Giwa, dan koda ka kadata namanta bai ciyuwa gareka sai da taron dangi Sulaiman Garko. Tabbas Nadiya ƙawar Mawaddat ce bakayi ƙarya ba, idan kuma kace zaka nuna wani giggiwa a wannan kadamin karan bana ne zai yi maganin zomon bana. Dan ka tabbatar da Mawaddat ce ta haifi Mawaddat, kasan kuwa tunanin zai iya zama duk iri ɗaya, hakama jarumtar. Ballema a yanzu da take a jingine a jikin matashin *_ZAKI_* na haƙiƙa ba arar suna ba irin ka. Gefenta ga *_DAMISA_* ƙi sabo. Sannan ga addu’ata biye gareta a dukkan motsinta. Ai nasha faɗa maka ni da ƴata da zuri’arta gaba ɗaya *_FURAR DANƘO_* muke, *_A SHEKARA ANA DAMU BAMU FARAU-FARAU_*. Idan kai acan ka wuni, ni kwana nayi. Maza ka sake shiri *_MAZAN_* ƙwarai da *_MACE_* mai kamar maza ne tafe bisa kanka ƙaramin biri……”
“Isma’illll!!!!!!”
Alh Sulaiman ya kira sunan Daddy cikin wata irin Mummunar tsawa mai razani. Kafin Daddy ya ce komai ya ɗora da faɗin, “Amma dai kasan zan iya karar da duk jama’ar asalin ƙauyen da ka fito bama kai kawai ba ko??!!!”.
Dariya Daddy ya ƙyalƙyale da shi tare da faɗin, “Ai ga fili ga mai doki nan Sulaiman Garko, zaka iya gwadawa idan har zaka iya, dan wlhy ba jama’ar garin jiƙamshi ba, koda ƙasar jiƙamshi ka taka da manufa saina karya ƙafafunka ta yanda bazasu ƙara ɗaukar gangar jikinka ba har gaban abada. Amma kafin ka tafi jiƙamshin ƙarar dadu ka tabbatar ka fara duba saƙo ga shi nan zai zo a hannun matarka shashasha ƙaramin biri abin wasan yara a tsakkiyar kasuwa”. Ya yanke wayarsa.
Haukacewa ne kawai Alh. Sulaiman baiyi ba da kalaman Daddy masu ƙona zuciya. A wani irin birkice ya ɗaga wayar ya naka a ƙasan tiles. Dai-dai nan amaryarsa ta shigo hannunta ɗauke da leda. A ɗan tsorace da ganin yanayin nashi ta ajiye ledar tana faɗin, “Saƙone aka kawo a baka, yanzu maigadi ya kaw….”
Yanda ya juyi a fusace ya hanata ƙarasawa. Har ya juya shima da nufin baida lokacinta sai kuma ya juyo tare da wani irin fisgar ledar. Zazzageta ya shigayi cikin tsumar jiki. Babu komai a ciki face Flash drive. Cikin rawar jiki data ruhi ya kai zaune daɓar yana mai janyo laptop ɗinsa ya saka flash ɗin jiki. Gaba ɗaya ya manta da kasancewar matarsa a wajen yay playing video ɗin da ke cikin Flash ɗin. Ba komai bane face fuskar mahaifiyar Lulu tana kuka da faɗin wannan shine kundin manyan laifuka na shi a ciki. Tana roƙon ko bayan babu ranta iyayensu su sani shine yayma Sultana fyaɗe….”
Ai bai ma kai ƙarshen video ɗin ba ya buga wata irin kuwwa da hankaɗa Laptop ɗin ƙasa itama ta kifu. Amaryasa data gama jin komai cikin firgita ta buga ihu itama tana neman hanyar fita a guje. Cikin tashin hankali yay tsalle ɗaya ya taɗota ta zube ƙasa. Idanunsa a rufe ya kai mata wata irin wariyar shaƙa. Tuni idanunta suka juye ta fara ƙaƙarin mutuwa.
“Mi kika ji?!! Na ce, “Mikika ji!!? Dan uban uwarki”.
Kanta take jujjuyawa alamar bataji komai ba. Wawan mari ya ɗauke fuskarta da shi ta bayan hannu da sake maƙureta. “Idan ma kinji ko kin gani wlhy wlhy wlhy ki zama kurma. Idan ba haka ba da hannuna zan kashe ki, na gina rami a tsakkiyar falon nan na bizneki. Kuma har abada babu mai sake jin labarinki ko tambayata ina kike. Baƙar mayya mai leƙe-leƙen masifaa!!”. Ya ƙare maganar da yarfar da ita ƙasa. Ya wuce bedroom ɗinsa a birkice. Babu jimawa sai gashi ya fito. Har lokacin tana kwance a wajen yabi takanta ya fice abinsa. Umarni ya bama maigadi akan kada wanda ya fita a gidan. Daga haka ya birka motarsa da kansa yau ya fice a bala’in guje….
*_★UK★_*
Cikin tashin hankali Lulu ke kallon Smart. Dan duk abinda ke faruwa tsakanin Alh. Sulaiman da matarsa akan idonsu ne kasancewar sun saka direct camara a jikin Alh. Sulaiman batare daya taɓa farga ba. Sun yi wannan aikinne kuma a lokacin da ya tafi jiyya bayan jami’an tsaro sun sake sa akan kidnapping ɗin Lulu da yayi. Sun haɗa baki da likitansa aka saka masa camara a gefen kunne ta wajen wuyansa a zuwan wani tabon theatre da akai masa ne a wajen wai na’urar na rike jijiyar kunnensa. Wannan aikin Uncle Yousuf ne, sun zaɓi saka masan ta yanda bazasu gansa ba sai dai suga abinda yake aikatawa saboda yanayi na yau da kullum irin na ɗan adam. Wanka da makamantan hakan. A kuma duk lokacin da zai shiga ɗaki da matansa ko aikata wata Masha’arsa da karuwansa sukan tsaida gani daga wajensu domin kiyaye dokar ALLAH. Ta wannan direct camara suke sanin duk wani motsin Alh. Sukaima batare da shi ya farga da hakan ba dan yana kallon abinda aka saka masan ne a yanda aka faɗa masa cewar tana riƙe jijiyar kunnesa da ta samu matsala.
“Wannan mahaukacin fa zai iya kashe matar nan. Ya kamata muyi wani abu”. Lulu ta faɗa cikin tashin hankali itama ganin yanda Kawun nata ya fita a hayyacinsa. Murmushi kawai Smart yayi yana ɗan lumshe idanu da zamewa ya kwanta. Kamar bazaice komai ba sai kuma zuwa can ya firzar da iska yana bata amsa da, “Babu abinda zai maita, wannan hargagin da kikaga yanayi na rashin mafitane kawai da ruɗanin da yake a ciki. Amma ba itace a gabansa ba yanzu Daddy ne da ke sai kuma mu da yake son sanin su wanene. Ina mai tabbatar miki yanzu haka gidan Daddy zai je”.
Da sauri Lulu ta ce, “What! Gidanmu fa kenan?” sai kuma ta fisgo computer ɗin gabanta ta sake buɗewa batare da jiran amsar Smart ɗin ba. Ilai kuwa sai ga Alh. Sulaiman na kwaɗa gudu a saman titi. Cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi a anguwarsu, a ma ƙofar gidansu. Sai dai ya gagara ƙarasawa saboda jami’an tsaro da ke zagaye da street ɗin ma gaba ɗaya musamman jikin gate ɗin gidan nasu. Wani irin duka ya kaima steering ɗin kamar zai fasa ihu. A haukace yay reverse ya koma ganin jami’an tsaron sun yo kansa…. Bata ma san lokacin data kwashe da dariyar data saka Smart buɗe idanu yana kallonta ba…
___________________★
Abubuwa tako ina suna cigaba da kwaɓema Alhaji Sulaiman Garko. Domin kuwa da zaman meeting na maganin matsala da yayi musu. Dan kullum a cikin yinsa suke. Kowace hanya sunbi domin ganin sun cutar da Daddy ko zuri’arsa al’amarin ya gagara. Yanda Daddyn ke zagaye da jami’an tsaro lamari ba’a cewa komai. Sun kai hari gidan su Smart shima dai, sai dai anyi rashin sa’ar samun gidan a baje sai masu aikin gini. Iya bincike kuma kowa a anguwar sai yace bai san inda suke ba a yanzun. Fahimtar kamar raina masa wayo sukeyi ya sakashi komawa gida rai a ɓace neman mafita. Kowa bai nema ba a matansa ya nufi sashensa kamar zai tashi sama. Wani irin kallon ɓacin rai yabi falon da shi, ganin yanda ya barsa a harmutsensa haka ya dawo ya tadda abinsa. Abinka da mai zuciya a kusa, tuni ransa ya sake ɓaci. A dai-dai nan Hajiya Turai ke shigowa sashen nasa. Ganin ko’ina a harmutse ga shi yanata faman huci ya sata zuba masa ido. Sai kuma cikin dauriya ta ce, “Alhaji lafiya kuwa kake miya sameka haka?”.
“A’a a cikin turnuƙun yaƙi nake? Ke ban san iskanci fa da rainin wayo”.
“Ikon ALLAH, ALLAH ya baka haƙuri da ga tambaya”.
Bai sake tanka mata ba, itama saita fara ƙoƙarin tattara falon. Taɓa Laptop ɗin sa da tayi ya sashi tunawa da Flash ɗin dake jiki. Cikin tsawa ya ce, “K bani ita nan!”. Bata musa ba ta miƙa masa zuciyarta na sake shiga mamakinsa. A fisge ya amsa. Sai dai me babu Flash ɗin a jiki. “Ina Flash ɗin jiki yake?”.
“Flash kuma? Ni banga wani Flash ba, a gabanka fa na ɗaga ta”. Wani irin kallon zan kashe ki na binne anan ya shiga binta da shi. Hannu ya miƙa mata alamar bani. Sai duk ta sake dabircewa. “Wai Alhaji kana lafiya kuwa. Wlhy ban ɗaukar maka wani Flash ba. A gabanka fa na ɗaga Lap-top ɗin nan ba wani waje naje da ita ba balle kace.”
Babu zato babu tsammani taji saukar mari har biyu. Kafin ta gama dawowa a hayyacinta ya sake miƙa mata hannu da tsananin tsawa yace, “Turai!! Bani”.
“Wlhy tallahi Alhaji ban ɗaukar maka komai ba. Wai yau ka fara zama dani ne? Koka taɓa ajiye abinka ka nema ka rasa da har zaka ɗaga hannu ka maran!”.
“An mareki ko zaki rama ne?”.
“Bazan rama ba, amma zan barka da ALLAH”. Ta faɗa tana ficewa fuuu. Mutumin naku tuni zuciyarsa neman fitowa take ta baki, amaryarsa da ya bari a falon nasa ta kuma ji komai ce tazo masa a rai. A harzuƙe ya nufi sashenta, babu ko sallama ya banka ƙofar ya shiga. Baiko kalli ƙanwarta dake gaishesa a falo ba ya wuce bedroom ɗinta kamar zai tashi sama.
“Wlhy aunty ba ƙazafi bane ba naga komai fa da idona, kuma na faɗa miki ƙanwar nan tasu data rasuce ma fa a video ɗin, ɗayar kuma ƙanwar tasu ce ta ɗauka mahaifiyar yarinyar nan da ake cema Lulu….”
Waɗan nan kalamai da suka nema fasa zuciyar Alh. Sulaiman ne ke fitowa da ga bakin amaryarsa. Abinda kuma yaji na tabbatar masa taga komai da komai kuma ta faɗa ma wadda suke wayar. Ta buɗe baki zata sake magana idonta ya sauka a kansa. Zabura tayi, kafin ya iso gareta ta kwasa da gudu ta shige toilet ta banko ƙofar. Yana dannawa tana dannowa har dai ALLAH ya bata sa’a ta murza key. Wasu manya-manyan ashariya ya fara mulmula mata yana jijjiga ƙofar tamkar zai cireta. Itako duk da a tsorace take faɗi take, “Wlhy ko zaka kasheni bazan bada ba”.
Ashariya ya cigaba da ingiza mata da tabbatar mata wlhy sai ya kasheta…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣4️⃣
…….Hankalin ƙanwarta da ke jiyosu a tashe ta dannama mahaifiyarsu kira. Tana ɗagawa ta sanya mata kuka da faɗin suzo dan gida babu lafiya. Ga mijin auntyn ta nan zai kasheta. Wannan kalmar ta kisa ta ɗaga hankalin mahaifiyar tasu, babu ɓata lokaci kuwa sai gasu sun iso. Iya ƙoƙari iyayenta sunyi Dan ganin ya kwantar da hankalinsa an sasanta komai amma yaƙi sauraresu. Ya kuma babbake ƙofa yana jiran ta fito. Dole mahaifinta yay kiran Baba Garko. Baba Garko yaso ƙin shiga maganar, sai da ya jiyo manya-manyan ashariya da munanan kalaman bakin ɗan nasa ta cikin waya sannan ya shiryo yazo. Karo na farko kenan da suka haɗu tun bayan badaƙalar auren Lulu. Da ƙyar aka fidda amaryarsa a gidan bayan yasha mari a hannun Baba Garko. Sam bakinsa bai mutu ba, faɗi yake sai ya kasheta idan bata bashi abinda ke wajenta ba. Itako tana rantsuwar bazata bada ba. Ana tsaka da wannan rikici itama Hajiya Turai ta fito ƴan aikinta janye da akwatuna. Bayan ta gaida Baba Garko cikin girmamawa yake tambayarta mike faruwa a gidan haka. Tana kuka ta sanar masa iya abinda ta sani, harda marin da itama yay mata. A cewarta tasan itama amaryar tasa babu abinda ta ɗauka masa, ya jefa abunsa wani wajene kawai ya huce a kansu, dan haka ita gida Sokoto zata wuce. Baba Garko bai hanata ba dan shi yama rasa abin cewa gaba ɗaya…..
*_★UK★_*
Watan Aunty Bilkisu ɗaya da sati uku cir aka sallameta da ga asibiti. A lokacin Lulu nada wata biyu da sati guda a UK. Doctor ɗin da ke tsaye akan lamarin aunty Bilkisu ce ta duba Lulu a ranar da tazo yin planing. Kamar wadda aka matsi bakinta a ranar sai take tsokanar AA dake ta tsale-tsallensa a ɗakin dan yanzu yayi ƙafa. Cikin ƴar dariya take cewa Lulu ta bata fine boy ɗin nan nata dan ita dai tana sonshi. Lulu tai murmushi kawai da faɗin cewa ta bata. Dariya ta sakeyi da cewar karfa daga baya tazo tace zata amshe, tunda taga ita matsoraciyace tana gudun samun wani cikin. Nan ma dai Lulu sai tai ɗan murmushi kawai ta basar gabanta ba faɗuwa dan Smart na a ɗakin sai dai waya yake yi. Likitar nan da neman magana ta sake cewa abinda ta saka mata bai dai bata matsala ko?. Da sauri Lulu takai dubanta inda Smart yake tsaye AA na jikinsa ya riƙe masa ƙafafu. Ido suka haɗa da shi, tai saurin janyewa zuciyarta na wani irin rawa, dan tunda ta yaye AA baida magana sama da ALLAH yasa ta samu ciki. Kanta ta dafe tana rumtse idanu, sai kuma ta ɗago ta kalla doctor ɗin da tuni ta maida hankali akan Nurse ɗin dake cirema aunty Bilkisu abu a jiki suna magana. Addu’a ta shiga yi a ranta ALLAH yasa kada parrot ɗin likitar nan ta sake magana. Yayinda take satar kallon Smart ta gefen ido. (ALLAH yasa mutumin nan bai ji ba) take ta ambata a zuciyarta. Lokacin da ya kammala wayar yana takowa inda suke jitake sayin takun nasa tamkar yana yinsa ne da bugun zuciyarta. Bai nuna mata yaji ba, duk da yanayinsa ya sauya. Dan ko kallonta baiyi ba ya ƙarasa gaban aunty Bilkisu rike da hannun AA. Tambayarta yake badai tajin komai ko. Ta tabbatar masa da Alhmdllh. Kansa ya jinjina cikin lumshe ido, tare da juyawa ga doctor yace yana son magana da ita. Cikin tashin hankali Lulu da ke kallonsu ta gefen ido ta ɗago gaba ɗayanta. Nan ɗin ma bai kalli inda take ba ya saɓi ɗansa a hannu sukabi bayan Doctor ɗin. Da sauri ta motsa zata bisu, aunty Bilkisu ta kirayi sunanta cikin katse mata hanzari. Dan ita sam bataji furucin Doctor ɗin ba lokacin hankalinta nakan Nurse. Dole Lulu ta dawo badan taso ba. Sai dai gaba ɗaya jitake komai ya tsaya mata cak, hatta iskar da take shaƙa da fesarwa bata gamsar da ita. Kusan mintina goma Smart ya dawo ɗakin, daga ƙofar ɗaki ya dakata yana faɗa musu su sameshi a waje. Aunty Bilkisu ce tayi ƙarfin halin amsa masa. Lulu kam jitai tamkar an ƙarasa zare mata jijiyoyin jikinta.
Sun samesa a inda yace ɗin, Nurses ɗin da sukaima aunty Bilkisu rakkiya biye da su. Suna tsaye har sai da suka shiga mota sannan suka juya ciki. Aunty Bilkisu ya kalla ta mirror yace ta saka belt, daga haka bai sake magana ba ya tada motar batare da yace itama Lulun ta saka ba. Hakan ya mata ciwo, dan in har zasu fita shi da kansa ma yake saka mata belt amma yau ko arziƙin ta saka ɗin ma bata da. Jiki a saɓule ta saka tana mai karanto sunayen ALLAH a ranta, zuciyarta fal tunanin mi yaje yayo a wajen doctor ɗin. Rashin amsa ya sata jan bakinta tai shiru. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso gidan, ya ɗauki ɗansa yay shigewarsa. Sai itace ta taimakama aunty Bilkisu da Iya Tabawa data fito dan ita suka bari a gidan. Baya falo sai AA kawai da ya fara karakainar ɓarnar da yafi ƙwarewa a kai. Da’alama anan ya ajiyesa ya shige. Dole ta cigaba da daurewa suka zube a falon suma. Suna nan zaune ya fito cikin shirin fita, tayi mamaki dan tasan a irin wannan lokacin yana a gida baya fita ko ina. Tana son masa magana tana tsoron ya yaɓa mata mai zafi. Duk da dai bai taɓa kwatanta hakan a gaban wani ba. Aunty Bilkisu ya cema tasha magani ta kwanta, da ga haka ya ɗauki AA suka fice.
“Wai shi wannan mike damunsa? Naga tunda ya gama wayar nan ya wani canja gaba ɗaya kamar wanda ke’a cikin ɓacin rai?”. Aunty Bilkisu ce mai maganar tana kallon Lulu. Murmushin ƙarfin hali ta saki da faɗin, “Ƙila wani abu mara daɗi aka faɗa masa a wayar aunty, kin sanshi da zurfin ciki. Idan bashi yaso a sani ba ba faɗa zaiyi ba”.
“Aike naga ma da sauƙi Mawaddat. Amma a sanin da naima Hydar akan shiru-shiru banyi zaton zai iya sakewa da mace haka ba. Dan da idan yana abu saika ɗauka yana jin ƙyanƙyamin mutane ne ma. Ka faɗa masa magana ashirin ya baka amsar ɗaya sauran in zata kasheka ne ma ta kasheka babu ruwansa”.
Dariya zancen aunty Bilkisu ya bama Iya Tabawa. Lulu ma sai tai murmushin ƙarfin hali kawai….
Tsahon lokaci basu dawo gidan ba. Lulu ta kasa samun nutsuwa sau uku tana kiran wayarsa bai ɗaga ba. Sai da ta gama galabaita da rashin dawowar tasu sannan sai gasu. Iya Tabawa ce ta amshi AA da yay barci, shi kuma ya shige ciki abinsa bayan ya ajiye musu abinda ya shigo da shi ya shige da sauran ciki. Taja mintuna kafin ta tashi tabi bayansa, dan ita dai kam da wannan fisge-fisgen gara ayita ta ƙare kawai yamayi komi zai yi yafi mata sauƙi. Ta samu har ya shiga wanka, dan haka ta zauna bakin gado zaman jiran fitowar tasa. Zuwa can kuwa sai gashi ya fito da bathrobe a jiki yana faman goge kansa zuwa wuyansa da ƙaramin towel. Kallo ɗaya yay mata ya kauda kansa. Gaban mirror ya ƙarasa ya fara shafa mai, dan haka ta taso jiki a saɓule cikin dauriya tana faɗin, “Wai mike damunka ne? Gaba ɗaya ka canja ko wani abu ya faru? Idan abinda kaji doctor ta faɗa ne dan ALLAH ka saurare ni na maka bayanin da zaka fahimta”.
“Anyi wani abu ne?”.
Ya faɗa kamar a gatsine”.
Rasama mi zatace masa tayi. Sai kawai tai tsaye ta zuba masa ido. Suna samun saɓani, amma bata taɓa ganin ɓacin rai a tattare da shi irin yau ba. Dan saɓanin da suke samu ƙaramine a take su shirya kuma. Amma wannan duk ya ɗaureta da jijiyar wuyanta. Harya kammala shafa man ya miƙe zuwa wajen kayansu bata sake iya cewa komai ba. Babu jimawa ya fito sanye da pyjamas masu laushi, turare ya fesama jikinsa ya haye gado abinsa tamkar ma ya manta da ita a ɗakin.
Da ƙyar ta iya furta, “Coffee fa?”. Dan yana shansa sosai. Batare da ya kalleta ba yana jan duvet jikinsa ya ce, “Naƙoshi.”
Zuciyarta tuƙuƙi take mata, dan haka cikin rawar murya ta sake faɗin, “Dan ALLAH ka tashi muyi magana, dan nasan wlhy abinda likitar nan ta faɗa ne ya ɓata maka rai, tunda kafin hakan ai cikin farin ciki muka fita, kuma ko’a can ma babu wani canji a gareka sai da akai maganar. Ni gask…..”
A wani irin fusace ya ɗago yana kallonta. Tuni idanunsa sun kaɗa jazur. Cikin kaushin murya da ɓacin rai ya ce, “Mawaddat bana son damuwa. Kinji nace miki wani abu ne? Kin tambayeni na faɗa miki babu komai, to mikike son nace miki. Please bana son hayaniya ki barni nai barci na. Idan kuma ɗakin kike so na bar miki ki cigaba da damuna”. Daga haka ya juya yay kwanciyarsa da sake jan bargo ya rufa. Jikin Lulu rawa ya farayi dan ɓacin rai. So take itama ta masa masifar amma ta kasa, ta rasa miyyasa take jin shakkarsa a yanzu har bata iya maida masa murtanin magana balle yin wani yunƙuri. Gaba ɗaya cika mata ido yake da wani irin kwarjini, girmansa take gani mai girman gaske da bayan mahaifinta da Uncle Yousuf bata ganin wani ɗa namiji da shi a duniya. Bata son ganin ɓacin ransa a yanzu balle ace itace ta ɓata masa. Ko yaya taga yayi fushi hankalinta tashi yake yi har sai taga sun shirya….
_____★
Sam babu daɗi a tsakaninta da mijin nata ɗan tsakanin nan, zai zauna yay wasa da yaronsa suyi hira da Iya Tabawa da Aunty Bilkisu amma ita banda ita. Ya ƙaurace mata a shimfiɗa, abinci ma idon su Aunty Bilkisu ke sakashi ya ci. Amma idan daga ita sai shine sai yace ya ƙoshi. Suna a wannan halin ya wuce Coventry wasa. Tafiyar tasa ta bata damar zuwa asibiti ta nunama doctor ɓacin ranta akan abinda ya faru da tambayarta su dama basu da sirri ne tsakaninsu da patient nasu, haƙuri ita dai doctor ta bata dan batai zaton al’amarin zai zama a haka da girma ba. Sannan ta faɗa mata bata san mijinta bai sani ba ai.
Kwanansa uku ya dawo. A ranar ne ta gama shirya sai dai suyi duk wacce zasuyi. Dan ta haɗa kayanta tsaff akan zata koma Nigeria. Kamar yasan shirin nata bai shigo gidan ba wannan karon sai dare. A yanayin gajiyen da yake yasa bai zauna ba suka gaisa da su aunty Bilkisu sama-sama ya shige ciki……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣5️⃣
……… Da kayan data haɗa na tafiya ya fara cin karo. Yay ma kayan kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Har ya gama wanka ya kimtsa bata shigo ba, duk da yaji hakan babu daɗi sai ya daure. Ganin bata da niyyar shigowa shi kuma yana bukatar shayi ya sashi mikewa ya fita da kansa. A falo ya sameta zaune ta zubama tv ido. Ɗan tsai yay yana kallonta na wasu sakkani, sai kuma ya ɗauke kansa ya wuce kitchen. Babu daɗewa ya dawo ɗauke da cup ɗin shayi, wucewarsa yay nan ma ya barta da ƙamshin turarensa. Takaicinsa ne ya turnuƙe mata zuciya, taji kamar ta fasa ihu. Sai kawai ta ɓige da sakin kuka mai cin rai. Wayarta ta ɗauka, tai tsai tana kallo da tunanin wanda zata kira ta sanarma damuwarta, sai kuma zuciyarta ke kwaɓarta da yin hakan. Wani gefe na bata shawarar gara taje suyi duk wacce zasuyi ita da shi amma karta yarda sirrinsu ya zama abin kasawa a fai-fai. Sannan ba lallai ne ba ta samu goyon bayan wani, musamman idan tai la’akari da yanda mutanenmu suka ɗauki haihuwa abu mai matuƙar muhimmanci. Wayar ta yarfar a kujera wasu hawayen masu zafi na silalo mata. Ita da wannan shariyar da yake mata gwara ya balbaleta da masifa kawai, idan yaso ma ya haɗa harda duka yafi sauƙi. Batun yanzu ba ta tsani ta samu saɓani da mutum ya mata shiru, gara a sanar mata ayi hayaniyar da za’ayi komai ya wuce, saboda ita bata iya riƙo ba sam. Shiyyasa tafi yarda da da’an mata ta rama kawai a wuce wajen sai wata kuma ta taso.
Aunty Bilkisu da ke karance da yanayinsu a kwanakin nan leƙowarta biyu tana ganin Lulu zaune a falon. Ana ukun ne ta sameta tana kuka. Shiru tai tana kallonta cikin nazari, kafin ta ƙaraso cikin dakin ta kai zaune a kusa da ita ta zari tissue ta miƙa mata. Lulu bata musa ba ta amsa ta share hawayenta. Sai dai duk da haka basu daina zubowa ba. Lokaci sosai ta bata ta rage nauyin zuciyarta da kukan kafin ta fuskanceta. Cikin tausasa harshe ta ce, “Wannan shine auren! Shine kuma haƙurin da iyayenmu ke yawan jaddada mana akan muyi idan za’a kaimu gidan aure da bayan an kaimu. Su maza haka suke zuma ne ga zaƙi ga harbi. Zaka iya kuma cin karo da kowanne a garesu a kowanne irin lokaci koda babu wani ƙwaƙwƙwaran laifin da kai musu. Mawaddat kada ki kalleni a matsayin yayar miji, kalleni a matsayin yar uwarki mace da tasan zafinki da sanin ma’anar kalar raɗaɗin da kike ciki. Minene ke faruwa tsakaninki da shi?. Karki damu ki faɗa min, zan koya miki dabarun da zaki cimmasa, dan nasan Hydar nada zuciya, kafiya, da taurin kai akan abinda yake ra’ayinsa.”
“Aunty ni ban san mina masa ba. Na tambayesa amma yaƙi faɗa. Har roƙonsa nayi bai saurareni ba. Ni gaskiya ina son na wuce gida bazan iya ba….”
A bazata batare da sun san yana a bayansu ba suka ji saukar muryarsa a kansu, “Ai dama bazaki san mi kikamin ɗin ba, gida kuma ga hanya nan a buɗe tunda dama shine burinki tun ba yanzu ba!!”.
A zafafe itama Lulun ta ɗago zatai magana aunty Bilkisu ta jinjina mata kai tare da jimƙe hannunta cikin nata alamar kar tace komai. Shirun tayi sai dai ta fashe da kuka. Tsaki yayi da juyawa zai koma dan dama kofin da ya sha shayi ya fito maidawa kitchen, da sauri aunty Bilkisu ta dakatar da shi da faɗin, “Hydar dawo ka zauna”.
“Aunty ni mizan zauna na mata, kina jin fa abinda take cewa. Dan taga na ƙyaleta bance komai ba har tanada bakin faɗama mutane zata wuce gida. To zuciya take tunanin ta fini ko mi?…”
“Hydar Please cool dawn mana. Nace ka zauna. Idan kuma Ammah kuke son na kira muku nikam sai na kirata. Maybe ita kufi jin maganarta”.
Ransa a ɓace ya dawo ya zauna. Sai faman sauke huci yake. Yayinda ita kuma Lulu take kuka. Sai da aunty Bilkisu ta basu mintina kamar uku zuciyoyinsu suka ɗan risina kafin tai gyaran murya kaɗan tana fuskantar Smart. “Aliyu mike faruwa? Kasan dai Mawaddat amana ce a hannunka, sannan ni shaida ce tanada haƙuri da ƙoƙarin ganin ta ƙyautata maka a matsayinka na mijinta da kiyaye duk wani ɓacin ranka. Shin miya kawo wannan fitinar a tsakaninku haka babu daɗi? Kuna ganin kunmin adalci abu ya faru kuna irin wannan tashin hankalin ina a tsakkiyarku. Wane laifi ta maka? Miya faru kake fushi da ita? Tunda ita ta tabbatar min bata san abinda tai maka ba…”
“Ai bazata sani ba tunda ta ɗaukeni wawa da bai san ciwon kansa ba….”
Cikin kuka Lulu da ke kallonsa ta ce, “Toni ya kake so nayi maka ne Aliyu. Na tambayeka kace ban maka komai ba. Amma kana fushi da ni. Ko magana baka son kayi dani, idan ka gaji da zamanmu ne ka sallaman na wuce tunda ai ba dole bane. Ni dama bance inayi ba balle kaji su bini da tsatstsaga….”
“Oh nine kazar kenan? Ai ba sai kin faɗa ba dama nasan ba ƙaunata kike ba. Dan baki da yanda zakiyi da ni ne kawai kike zaune. Sai dai ban san ƙiyayyar da kike min ɗin takai girman haka ba, har ki guji haihuwa da ni. Na farkon dama ALLAH ne yayi maganinki ya samar da shi a lokacin da bakiyi zato ko tsammani ba, shine yanzu kika bi hanyar takaita ni. To sai ki sake ɗaura ɗammara dan wannan batai dai-dai da ke b…..”
“Ya ALLAH Aliyu…”
Aunty Bilkisu ta katseshi cikin tashin hankali. Dole yay shiru shima yana hucin. Yayinda Lulu ke kukanta ita dai. Shiru falon yayi kusan mintuna biyu sai ajiyar zuciyoyinsu sannan aunty Bilkisu ta sake dubansa. A nutse ta ce, “Kai waya gaya maka bata son haihuwa da kai Hydar? Banji daɗi wannan furucin naka ba sam gaskiya”.
“Gaskiyar kenan ai aunty, inda tana son haihuwa dani bazataje tai planing babu sanina ba. Da haka zamuyita tafiya ni ina tunanin akwai matsala ita kuma tana cutar dani. Da yake bani da hakkinta sai gashi ALLAH ya sanar dani ta hanyar likitar da taje ta dubata. Ni na taɓa cemata bana son yarane? Gidanmu mu kusan talatin aka haifa, yanda na tashi na gammu nima haka nake fatan tara zuri’a. Amma shine zata zaluntan….”
“Niba azzaluma bace, kuma nima bance bana son haihuwar ba ai…”
“Ƙarya kike yi wlhy, idan ba zalunci ba mi kikayi? Da lafiyata da ƙuruciyata ki cutar dani ta hanyar katangeni da ganin jini na. Ke wlhy kika sake maidamin magana zan fasa bakinki ne har sai haƙoranki sun zuba. Bana son raini ki shiga hankalinki kar kiga ina ƙyaleki ki ɗaukeni wani banza can!!….”
A hargitse Lulu take dubansa. Zatayi magana Aunty Bilkisu ta hanata. Shiko sai huci yake yi dan ya gama kaiwa wuya. Abinda Lulu bata sani ba Smart ya tsani yana magana ana maida masa. Musamman idan shi akaima laifin yana sake harzuƙa ne. Duk yaran gidansu sun san wannan halin nasa, shiyyasa suke kiyaye wa. In ko kai kuskuren dagewa akan dole sai ka masa bayanin da zaka fidda kanka zai iya maka dukan hauka ne ya bar uwarka da jiyya. Wannan itace babbar matsalarsa, idan yay ƙololuwar fushi baya iya controlling temper ɗinsa sam. Shiyyasa yake da ƙoƙarin kauda kansa akan abubuwa. Ganin yanda ya fusata ya saka aunty Bilkisu cewa suje su kwanta da safe sa ƙarasa. Shi ya fara tashi fuuu ya wuce, dan haka ta hana Lulu tashi. Nasiha ta fara mata da sanar mata halinsa na son rashin maida murtani ko bama kai kariya. Dan shi idan akai masa laifi ko bayani wani lokacin baya buƙatar ai masa. Gara ka masa banza idan ya gama hawa da saukar zai huce da kansa ya dawo ya binciki gaskiya in ma hukuncinne ya maka. Ta nuna mata kuskurenta tare da bata shawarar taje ta cire abinda ta saka ɗin. Haihuwa ai komai na ALLAH ne. Ayi fatan kawai ALLAH ya bada masu albarka. Lulu taji daɗin nasiha da shawarar aunty Bilkisun, dan haka ta ɗan ji zuciyarta ta rage mata nauyi.
Koda ta shigo ɗakin kwance ta samesa. Batai magana ba ta shiga toilet tayi wanka ta gyara jikinta. Kamar yanda sukeyi a tsakanin nan kwanciyar kai da ƙafa haka ta kwanta yau ma. Ta lulluɓa da bargon data ɗakko. Duk abinda take yana jinta, amma ko motsawa baiyi ba. Sai can cikin dare sosai ya tashi yayo alwala ya zo ya kama salloli. Sai da ya ji zuciyarsa ta samu nutsuwa da karatun Alkur’ani sannan ya tsagaita. Ganin asubahi ta gabato ya haƙura bai kwanta ba har sai da yay sallar asubahi. Alerm ne ya tada Lulu, dama haka yake mata tunda suka samu saɓanin. Kafin ta fito bayi ya haye gadon yay kwanciyarsa…
Ranar yini yay barci, dan sai azhar ya tashi. Babu kowa a ɗakin sai shi kaɗai. Yay wanka ya shirya cikin ƙananan kaya marasa nauyi. Suna falo zaune Iya Tabawa na basu labarin sanda suna ƴammata Lulu na kwasar dariya kamar ba ita tasha kuka jiya ba ya fito, sam ita bata da riƙe abu, shiyyasa idan aka riƙeta take jin zafi. Da gudu AA dake wasa ya nufosa. Cak ya ɗaga yaron sama yana mai sumbatarsa cike da jin ƙaunarsa. A haka ya kai zaune cikin kujera suna dariya shi da AA ɗin da yakema cakulkule. Iya Tabawa ya fara gaisarwa sai aunty Bilkisu. Ya tambayeta yaya jikin tace Alhmdllh sai fatan komawa gida lafiya. Murmushi yay da faɗin, “Ai keda Nigeria sai nan da shekara ɗaya”.
Idanu ta waro sosai da faɗin, “Shi kuma mijin nawa kuyi yaya da shi?”.
Cikin kauda kai da taɓe baki ya ce, “Uhm su miji”.
Kafin aunty Bilkisu ta sake cewa wani abu a fisge Lulu tace masa “Good Afternoon”. Kallonta yayi shima a karo na biyu cikin ɗauke kai yace, “Afternoon” a taƙaice. Daga haka babu wanda ya sake kula ɗan uwansa. Abinci ma sai da aunty Bilkisu ta zungureta ta tashi ta kawo masa. Batai zaton zaici ba, amma sai taga yaci sosai yana bama AA. Bata san yayi matuƙar kewar girkin nata ba ne. Basarwar da yake ɗin ma ta dole ce. Haka ya ƙarasa yinin nan a gida yau ko waje bai leƙa ba har washe gari. Washe garin ma sai zuwa yamma ya fita training center ɗinsu……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣6️⃣
…….Kwana uku ya ɗan fara hucewa a dalilin murar zazzaɓi da Lulu ke fama da shi. Duk da dai tana nuna ita ƙalau take. Sai da murar tai mata tsanani ne ta haƙura takai zaune. Mata da miji sai ALLAH sai gashi yana tattalinta da matsa mata tasha magani. Harda haɗa mata shayin kayan ƙamshi da kansa. Idan yaga AA zai takura mata ya ɗaukesa ya kaima Iya Tabawa. Ya bata kulawa sosai harta samu sauƙi. Da ga haka aka shirya kamar basu ba aka koma nunama juna soyayya da tattali. Sai aikinsu da suka saka a gaba. Ita aunty Bilkisu ma sai abin ya koma bata dariya. Shiyyasa dai akace duk wanda ya shiga tsakanin mata da miji ya matse. Dan zasu shirya ne su barsa a ciki. A haka kwanaki suka cigaba da shuɗawa mura na damun Lulu akai-akai. Ita abin har mamaki yake bata dan bata cika yawan mura ba a da. Sai dai ta danganta yanayin da sanyi da ake yi sosai harda dusar ƙanƙara.
Wasan su Smart na tafiya cike da nasarori da kalubale. Yayinda sunansa keta ƙara cigaba da amsa kuwa saboda yanda yake zura ƙwallaye a raga babu ko ɗar. In dai za’a kirayi sunan wani yaro mai tashe a wannan ƙarnin a harkar ball idan sunansa baizo na ɗaya ba dolene yazo ana biyu. Ballema ALLAH ya bashi farin jinin da akan ambacesan a farko. Sam baya wasa da addininsa. Sannan tsaye yake akan Lulu itama dan har yanzu shine mai ɗora mata karatu datai matuƙar maida hankalinta a kai. Wani lokacin kuma aunty Bilkisu ke ɗora matan.. A gefe kuwa sun matuƙar saka rayuwar Alh. Sulaiman a gaba, dan a yanzu haka ana tsaka da dambarwa ne tsakaninsa da amaryarsa akan Flash. Anyi-anyi ta bada taƙi. Yayi haukan yayi hargagin yayi kurarin duk da tana a gidan nasu tayi kememe. Hajiya Turai dai ce ƴaƴanta suka dawo da ita. Acewarsu sai da Mahaifin nasu ya bar mata gidan badai ita ta bar masa ba. Dan babu kunya suka dinga yaɓa masa magana musamman ma Tajuddeen, Alh. Sulaiman ranar harda hawayen baƙin ciki. Bai taɓa tunanin soyayyar da yakema Tajuddeen zai iya kallon tsabar idonsa ya masa rashin kunya haka ba, al’amarin ya girgiza zuciyarsa kam..
(Abinda kayi dole ai maka ai dama🚴🚴🚴😂).
*_NIGERIA_*
Watanni kusan huɗu kenan abubuwa na’a rincaɓe musamman a ɓangaren Alh. Sulaiman Garko. Dan anata musu tsinci ɗai-ɗai na masifa ta yanda gaba ɗaya kasuwar tasu ma ta tsaya cak. Ga manyan kayansu da ke gaf da zuwa Najeriya ɗin. Duk yay wani iri da shi duk da har yanzu ma shi bako a fara taɓashi ba. Dan ko’a cikin yaransa kaf babu wanda aka taɓa. Sai aminansa da Hon. Nakowa kawai ya rage sauran duk suna hannun hukuma anyi ram da su. Kullum cikin kiran Daddy yake yana masa barazana. Shiko Daddy na maida shi mahaukaci da naɗe komai a waya tare da kunnashi. A gefe ɗaya ga al’amarin amaryarsa da yaƙi ci yaƙi cinyewa. Burinsa kawai ya amshi Flash ɗin hannunta koda zai kasheta ne shi babu ruwansa. Tayi-tayi ya saketa kuma yaƙi. A randa yaje har gida ya cima mahaifinta mutunci ta tabbatar masa anzo gaɓar da take jira, dan haka a ranar ta aike ma su Baba Garko da video. Da kanta ta shirya taje har gidan ta danƙama Baba Flash. Har wulaƙanci Dada taimata saboda taje ta gaida amarya da duba yaranta. Ita dai bata tanka mata ba har Dadan tayi ta gama san ranta. Bayan wucewarta ne Dada ta nufi wajen Baba Garko. Ta sameshi da ƴan biyunsa da sukai kuɓul-kuɓul gwanin sha’awa. Takaici kamar zai tsayar mata da numfashi amma ta danne da ƙyar. Dama bata taɓa ɗaukar yaran ba tunda aka haifesa, dan haka yanzun ma kallo ɗaya tayi musu ta ɗauke kanta. Ko’a ƙwallar rigar Baba Garko, dan ya jima da fahimtar bakin ciki take da yaran. Sama-sama ya amsa mata gaisuwa ya cigaba dama yaransa wasa kamar ma ya manta da ita. Hakan ya sake Zafafa mata zuciya taji ta tsani yaran fiye da ko yaushe. A cikin tunzura ta ce, “Amma dai Alhaji bai kamata ka fifita rayuwar ƴar wasu akan naka ba. Yanzu yarinyar nan ta gama fetse mana yaro da iskance-iskanceta ta dawo tana mana barikanci. Ni na rasa mi Sulaiman yayi maka haka da zafi ne. Kabi ka tsangwamesa babu laifin tsaye babu na zaune. Idan ma maganar Mawaddat da Tajuddeen ce ya kamata ace ta wuce tunda dai tana gidan mijin da kuke son ganin nata da shi yanzu ai ko”.
Idan ɗakin ya tanka Baba Garko ya motsa, hakan ya sake harzuƙa Dada. Miƙewa tayi a fusace zuwa gabansa ta ɗauke Flash ɗin dake ajiye kusa da shi. Nan ɗin ma bai tanka mata ba harta fice, bai kuma nuna damuwa da ya bita akan flash ɗin ba ya cigaba da yima yaransa wasa. Hajiya Dada kam da masifa ta nufi sashenta. Harta ɗauki waya da nufin kiran Alh. Sulaiman akan yazo ya amsa sai kuma ta ajiye tana faɗin, “Bara dai naga wai ubanmi akema wannan tashin hankalin ne a ciki.” Ta ƙwalama mai aikinta kira. Jiki na rawa ta iso, a gabanta ta zube cike da girmamawa. Umarnin ɗauka mata tab.. a ɗaki ta bata. Babu jimawa ta dawo ɗauke da tab.. ɗin. Ita ta saka mata flash ɗin. Cike da gadara da ƙasaitar mulkin masu akwai Dada ta amsa ana wani gyara zama da busa iska tace mai aikin ta kawo mata lemo. Ita dai mai aiki umarni take bi.
Fuskar data fara bayyana ta saka ƙirjin Dada bugawa, jikinta ya fara tsumar kewa. Mawaddat ɗinta ce, yarinya mai hankali, mai sonta da ƙaunarta, sai dai ita kullum tana a cikin hantararta ne saboda tana ce mata kaza ba daidai bane kaza ne daidai. Kalaman Mawaddat suka cigaba da jan hankalinta kafin kace mi ta jiƙe sharkaf da zufa. Maimakon hasken ɗakin ta koma ganin duhu. Tun tana iya jin sauti da motsi har komai ya tsaya mata cak sai razanannen ihunta daya karaɗe kunnuwan duk wanda ke a kusa da sashen nata. Rige-rigen shiga masu aikin nata suka shiga yi inda take, sun sameta wanwar a ƙasa kofin lemon da aka ajiye mata ya kife da alama ma a kansa ta faɗa. Duk da hankalinsu ya tashi da ganin a yanda take sai da suka ɗauki tab.. ɗin suka kalla abinda ya razanatan. Yayinda mai tausayin cikinsu ta fita a guje kiran Baba Garko. Ai suma sai suka ƙare da ƙwalla ƙara a dai-dai shigowar Baba Garko da amaryarsa, dan tana tare dashi sanda mai aiki taje kiransa….
An ɗauki Dada babu alamar rai a tattare da ita ga jini na zuwa ta inda gilashin kofi ya jimata ciwo. Shi kansa Baba Garko a kiɗime yake dan bata taɓa kasancewa a irin hakan ba duk wannan rikicin da akeyi. Iyaka dai ta suma da’an zuba mata ruwa ta farfaɗo. Amma yau babu abinda basu gwada mata ba ko motsi. Da tab.. ɗin ya fita a hannunsa, dan yasan koma mi ya sakata a wannan halin bazai kasance ƙaramin ba.
Cikin ƙanƙanin lokaci labari ya isa kunnen ƴaƴanta da jikoki. Kafin wani lokaci asibitin da aka kaita ya cika da Garko family, zuri’ar Uncle Khamil dake Abuja ne kawai babu suma suna tafe sai na auta dake a Saudiyya. Har zuwa washe gari ba’a samu kan Dada ba, dan haka hankalin kowa ke’a tashe. Hatta shi uban gayyar a wannan karon hankalin nasa a tashe yake. Dan koba komai fa yana son matarsa, sannan itace uwar ƴaƴansa. Tun shekarun ƙuruciya suke tare har zuwa tsufa da daɗi babu daɗi tana zaune da shi. Washe gari zuwa sha ɗaya na safe auta ya iso tare da nasa iyalinsa, tamkar shi Dada ke jira ya iso ta farfaɗo, sai dai fa numfashin farko da taja ta fesar da jini ta fesoshi. Wani sabon tashin hankalin kenan, dan likitocin ma sun kasa musu bayani, sai kai-kawo da shigi da fici sukeyi. Duk wanda suka tunkara sai dai ya zame da faɗin yana zuwa. Duk wannan abun da akeyi babu Alh. Sulaiman sai ƴaƴansa da uwar gidan sa. Karan farko da Tajuddeen yaji baƙin cikin halin mahaifin nasa. Shin wai minene na wannan gabar, a ganinsa mahaifiya ai tafi gaban wasa. Dada na a irin wannan yanayin har yace yanada wata hujjar cigaba dayin gaba. Duk wanda yaga Dada a jiya zuwa yau dolene ya tausaya mata. Shi kansa Baba Garko ya ajiye makaman yaƙinsa harda hawaye yake da sambatun ta tashi dan ALLAH kada ta tafi ta barsa. Cikin ɓacin rai Tajuddeen ya dannama ubansa kira. A lokacin yana ɓoyayyen Companyn sa suna tattaunawa da yaransa malami da wasu abokan cinikayyarsa mazauna Legos akan kayansu da suka iso Nigeria a daren jiya. Sai dai sun rasa yanda zasu fidda kayan daga bakin ruwa saboda kamar fa an saka musu ido… Yana ɗaga wayar Tajuddeen ya fashe masa da kuka cikin masifa yake faɗa masa “Yanzu nan Dad har kanada lokacin nishaɗi haka mahaifiyarka kwance ranta a hannun ALLAH tana aman jini likitoci tun daren jiya tsaye a kanta. Anya kuwa kana fatan gamawa da duniya lafiya Dad. Ace iyayenka ne abokan gabarka. In dai dan ni kakeyi toka ajiye dan nikam dai na haƙura da Mawaddat koda ace sonta zai zamar min ajalina. Duk ƴan uwanka gasu nan har wanda basa ƙasar kai kaɗai ne ka fita zakka a cikinsu saboda son zuciya. Idan ta mutu sai kazo zaman gaisuwa ai” ya faɗa yana yanke kiran wani irin kuka mai cin rai na kufce masa…
*_★UK★_*
…..A dalilin wayar Tajuddeen da mahaifinsa su Lulu suka san halin da ake ciki. Domin suna tsaka da ganin zaman meeting ɗin Alh. Sulaiman da abokansa ta direct camara ɗin su. Hankalin Lulu ya tashi matuƙa, dan koma minene ya faru Dada ba abar yardawarta bace ba. Kuka ta fara cikin tashin hankali ta shiga neman layin ƴan uwa. Da kyar ta samu Uncle Amin ya ɗaga. Cikin kuka take faɗin yanzu nan Dada na’a irin wannan halin amma babu wanda ya faɗa mata. Lallashinta Uncle Amin ɗin ya farayi akan ta kwantar da hankalinta tai mata addu’a daga inda take. Amma ina Lulu taƙi saurarensa. Shima Smart ɗin ta matuƙar tayar masa da hankali, dole ya saya mata ticket dan bazai juri ganinta a haka ba. Sai dai ita kaɗai zata taho banda AA. Ta barsa wajen Iya Tabawa da aunty Bilkisu da har yanzu bata kammala ganin likita ba duk da tana a gida lokaci-lokaci dai take zuwa ana dubata asibitin……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣7️⃣
…….Uncle Yousuf da kansa yaje ɗaukar Lulu airport. Da ga airport ɗin kuma asibiti suka wuce kai tsaye. Ba ƙaramin girgiza zuciyarta tayi da ganin kowa da kowa na asibitin ba. Ashe ƴan Saudiyya ma har sun ƙaraso. Kasa haƙuri tai sai da ta leƙa Dada ta window. Dan an hana kowa shiga wajenta Baba Garko ne kawai ya shiga bayan likitoci sun sami kanta da ga aman jinin da take yi. Kuka sosai Lulu keyi da ya sake ɗaga hankalin duk wanda ke a wajen. Uncle Taheer Auta ne ya kama hannunta suka bar wajen, da ga gefe ya zaunar da ita yana lallashinta akan ta daina kuka addu’a Dada ke buƙata a yanzu. A hakama an samu kanta ba kamar da safe ba. Wannan ɗan lalashin da autan Dadan ya mata ne ya ɗan saka mata nutsuwa kaɗan ta rage kukan da take yi. Lokacin da zasu wuce gida tace ita a barta anan zata kwana. Hajiya Turai mahaifiyar Tajuddeen ce tai ƙarfin halin cemata, “A’a Mawaddat kema kulawar kike buƙata ai a wannan halin da kike ciki. Ga tafiya mai nisa kinyo”. Da yawan ahalin wannan family sun san ALLAH ya bama Hajiya Turai baiwar gane ciki koda ƙarami ne, dan haka kowa ya fahimci abinda take nufi akan Lulu ballema duk mai lura yaga Lulu yasan tana da ciki saboda illahirin halittun jikinta sun nuna hakan duk da kuwa akwai jin daɗi da samun kwanciyar hankali. Abinda bata sani ba hatta Iya Tabawa ta jima da fahimtar tana da ciki, tayi gum da bakinta ne kawai har ya bayyana kansa. Ita kanta aunty Bilkisu cikin kokwanto take magana ce kawai batayi ba. Amma har so tai ta tseguntama Ammah da ga baya kuma dai tai shiru dai. Lulu dai ba fahimtar Hajiya Turai tayi ba, sai dai babu yanda zatai ta yarda ta bisu. Kasancewar motar Hajiya Turai ɗin ta shiga sai kawai ta wuce da ita can gidansu (Gidan Alh Sulaiman kenan).
Alh. Sulaiman da tun wayarsa da Tajuddeen ransa ke’a ɓace yana zaune labarin zuwan Lulu Nigeria ya sameshi. Baida niyyar zuwa asibitin duk da baƙaƙen maganganun da ɗan cikin nasa ya faɗa masa sun kartar masa zuciya amma jin abar farautarsa a kusa da shi ya sashi niyyar zuwa. Sai dai bai baro Companyn nashi ba sai dare sosai saboda bada ƙafa. Sun riga sun gama shirya yanda zasu sace Lulu shida yaransa. Dan haka kai tsaye asibitin ya nufo. Sai dai ya samu kowa ya tafi sai ƙanwar Baba Garko kaɗai da ke tare da Dada. Inna Sadiya nada labarin komai na tsakanin Sulaiman da iyayen nasa, dan haka ta kallesa sheƙeƙe ta watsar, gaisuwar tasa ma sama-sama ta amsa masa. Duk yanda yaso jin wani abu daga gareta bata kulashi ba. Dole ya kama gabansa yana jan tagwayen ƙwafa da jin kamar ya make banza ya wuce. Yana fitowa yay kiran yaronsa Malami. Ya sanar masa su rabu zuwa gidan Daddy da Uncle Yousuf dan Lulu bata asibitin. Sun amsa masa da girmamawa, duk da sun san tsaron dake zagaye da gidajen daya faɗa ɗin, daga haka ya wuce gidansa shima. Koda ya iso bai nema matarsa ba kamar yanda itama ba shiga sabgarsa takeba a yanzun, dan tace zaman ƴaƴanta kawai takeyi ita kam dan ya gama fita mata a rai kasancewar amaryarsa ta sanar mata komai. Dan bayan dawowarta ƴaƴanta mata yayun Tajuddeen da ita sunje gidan su amaryar tasa domin lallashinta itama ta dawo ta nuna musu ai itakam tabar gidan nan har abada. Da suka matsa ne taja Hajiya Turai gefe ta sanar mata komai tare da nuna mata video ɗin nan. Hankalinta ya tashi matuƙa, dan itace ma ta bata shawarar ta kaima su Baba Garko videon inba haka ba mijin nasu zaibi duk wata hanya ya kwacesa a hanunta. Ba ƙaramin ruɗani Hajiya Turai ta shiga ba a week ɗin da ya gabata, da ƙyar ta iya tausar zuciyarta ko yaranta bata sanarmawa ba har yanzu.
Zuwa cikin dare jikin Lulu ya ɗume da zazzaɓi, kasancewar kwana biyun nan haka take fama sai bata damu ba. Ta dai sha magani ta kwanta duk da tana jin kewar mijinta ta taushi zuciyarta, sai gabannin asuba zazzaɓin ya saketa. Tana idar da salla kasa haƙuri tayi ta ɗora layinta na Nigeria akan waya. Smart ta fara kira. Bugu ɗaya ya ɗaga mata. A tare suka sauke nannauyan numfashi. Kafin a hankali ya fara furta, “Kin san ko yanda kika bar zuciyata cikin barazana da tashin hankali Baby luv. Tunda kika sauka nake jiran kiranki amma shiru har na fara jin nauyin yawan kiran da nakema Daddy da Uncle Yousuf.”
“Kayi haƙuri”.
Ta furta a hankali. Ajiyar zuciya ya sake saukewa da faɗin, “Ya zanyi, na haƙura. Ina dai fatan babu wata matsala ko? Dan wlhy gaba ɗaya na kasa nutsuwa duk da nasan wawan baiyi zaton kina gidansa ba”.
Murmushi Lulu tayi har yana iya jiyo sautinsa. Cikin ƙara tausasa harshe ta ce, “Bayan ka bashi ƙafa taya zai iya gano ka. Dolene na bama wanda ya saka maka suna Smart ƙyauta gaskiya. Mutum yana nemana ruwa a jallo amma ka turoni gidansa na kwana kuma. Sannan kada ka manta kawuna ne kake cema wawa”.
Ƙaramar dariya yayi shima. Ya ce, “ALLAH sarki masu kawu yi sorry. Sannan banda wata mafita sai hakan ai. Dan nasan bazai taɓa kawoma ransa zaki zo gidansa ki kwana ba. Yanzu dai sai kiyi taka tsan-tsan kuma.”
“In sha ALLAHU mijina. Jiya gaba ɗaya kewarka ta hanani isashen barci”.
“Uhm kamar da gaske. Ni ban san daɗin baki. Ina Aliyu yaga wannan matsayin. Ke dai kawai kice tsoro ya hanaki barci kina a gidan dodoki”.
“Oh hakama zakace ko? Shikenan ai zan rama. Bazan ma dawo ba sai bayan wata tara kama kanka”.
Dariya sosai yakeyi da faɗin, “Haba Baby luv ki tausayamin mana. Ni kaina kin ganni nan yanzu haka nama kasa kwanciyar sai lissafi nake da kallon hotunanki kawai. Na gayyato Baban Ammah ya tayani kwana ya addabeni da ɓuruntu.”
Cikin dariya ta ce, “Kai miya kaika wannan gangancin siyen gida a sama.”
“To yana iya kewar Mamansa ta isheni ne. Ni da ƙyar ma idan zan iya haƙuri ban taho Nigeria ɗin nan ba”.
Idanu ta waro sosai kamar tana gabansa. Ta ce, “Are you serious zaka iya barin wannan kwallon ka taho Nigeria?”.
“Humm yarinyar nan kina wasa da Aliyu ko? Zan baki mamaki”.
“A’a A’a nagode basai ka bani ba. Ai nasan zaka aika wlhy yi zamanka na yafe. Nima ba jimawa zanyiba ai. Yanzu dai ina son naje naga Ammah yaya za’ayi?”.
“Kefa rigimarki yawa gareta Mrs Mawashi. Keda ake ɓoyonki ina kuma zaki je yawo?”.
“Zuwa wajen uwata ne yawo. To nidai kasan yanda zakai dani gaskiya”. Ta faɗa cikin shagwaɓa har yana iya jiyo sautin yanda take buga ƙafa ƙasa.
“Kirufamin asiri Baby luv nayi barcina lafiya, kinga dai na sakama raina haƙuri tunda kika taho ko kuka banyi ba”.
Sosai Lulu take dariya. Ta ce, “Kuka fa?”.
“Eh mana, na dai zama kalar tausayine kawai ko wanka yau ma bazanyiba. To in nayi wazan mawa baƙya kusa”.
Dariya ta sake ƙyalƙyalewa da shi. Smart ɗinta kenan Zuma ga zaƙi ga harbi. Duk wanda kake buƙata za’a sayar maka akan farashin da ya dace. Sun jima suna hirarsu kafin ta tashi tayi shirin zuwa asibiti. Dan bazata iya sake komawa barci ba….
★Yaran Alh. Sulaiman nacan sun kasa sun tsare a tituna jiran fitowar Lulu da ga gidansu ko gidan Uncle Yousuf. Anan ko su har sun fice gidan Alh. Sulaiman sai fitar motar matarsa ya jiyo. Ƙwafa yayi dan yayi alwashin koya mata hankali itama dan yasan ita ke zuga masa yara suna mai rashin mutunci. Ranar matan sun masa akan dawowarta gidan. Jiya kuma Tajuddeen ya masa akan Dada. Bai damu da fitar tata ba dan yasan asibiti ta wuce. A asibiti sun samu jikin Dada yau dai Alhmdllh, da sauƙi irin na malam bahaushe da ake faɗi. Amma dai har yanzu bata gane komai, sai ambaton sunan Sulaiman da take a hankali hawaye na ziraro mata. Duk wanda ya shiga dubata sai ya fito da mamakin yanda ta damu da al’amarin yayan nasu Sulaiman haka, bayan rashin mutuncin da yake zuba musu salo-salo. Sai da ta koma barci ne Baba Garko ya ce iyayen su sameshi gaba ɗaya a gida. Ganin haka sai itama Lulu tai kiran Smart kawai akan zuwa wajen Ammah. Sai da yay ɗan jimmm sannan ya amsa mata da “Naga dai kin matsa da ganin Ammahn nan, ɗan bani 10minut haka”.
Baki ta murguɗa masa tamkar tana gabansa….
*_GARKO HOUSE_*
Ƴaƴansa ne gaba ɗaya. Alh. Sulaiman da wanda suka rasu biyu mahaifiyar Lulu da Sultana ne kawai babu. Sunyi kusan zaman mintuna huɗu kafin ya fito. Bayan yakai zaune suka sake gaishe da mahaifin nasu. Da kai ya amsa musu yana gyara zama dan zuciyarsa sam babu daɗi. Sai da ya gama ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya kafin yay gyaran muryar da ta sakasu sake maida hankalinsu garesa.
“Na taraku anan ne a dalilin abinda yay sanadin kwanciyar mahaifiyarku asibiti duk da ni har yanzu ban san minene ba shiyyasa na buƙaci ganinku mu gani tare dan zata iya yiwuwa nima na tsinta kaina a yanayin da yafi nata ma…” cikin tashin hankali da ruɗani duk suke kallonsa. Bai damu ba ya cigaba da faɗin, “Nasan wasunku sun san rikicin dake tsakanin ɗan uwanku da matansa wasu basu sani ba. A watannin da suka gabata rikicin da bamu san tushensa ba ya ɓarke a tsakanin Sulaiman da matansa su dukansu har suka wuce gida. Sai daga baya uwar ƴaƴansa ta dawo amaryar da al’amarin yafi tsamari a kanta taƙi ta koma. Na barsu ne naga iya inda abin nasu zai kai sai kuma gashi jiya ta samemu anan gida. Flash drive ta kawo mana ta tace shine sanadin rikicin nasu. Da ga haka batai mana wani ƙarin bayani ba ta tafi. Bayan wucewartan ne mahaifiyarku tazo ta ɗauki Flash ɗin ta wuce da shi sai mai aikinta ta isarmin da saƙon gata can ta faɗi babu rai. Duk abinda zai saka mahaifiyarku a wannan mummunan yanayin bazai kasance mai sauƙi ba. Shiyyasa tun jiya na kasa dubawa ni kaɗai na zaɓi mu duba tare da ku”. Ya ƙare maganar yana jawo tab ɗin Dada da har yanzu flash ɗin ke a jiki. kusa da shi duk yay musu nunin su dawo. Haka suka zauna wasu kusa da shi a ƙasa wasu a kujera. Babu wanda zuciyarsa bata kaɗa ba a lokacin da fuskar marigayiya Mawaddat ta bayyana. Kafin sukai karshen videon babu wanda jikinsa baya rawa a cikinsu, ga hawaye duk ya cika musu idanu. Auta da yafi kowa shaƙuwa da Sultana a gidan baima san sanda ya fashe da kuka ba tamkar ƙaramin yaro. Kasa jurewa Baba Garko yayi ya miƙe jikinsa na karkarwa. Sai dai dole sukai saurin riƙosa saboda hajijiya dake neman zubar da shi a ƙasa, shima sai kawai ya fashe da kuka. Kukan mahaifin nasu ya sake tayar musu da hankali. Suma duk suka fara sharar hawaye……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣8️⃣
………Kiran Smart ya saka Lulu tashi ta koma gefe. Kafin ma tace wani abu ya furta, “Akwai matsala fa Baby luv. Dan Kawunki ya baza yaransa sosai nemanki. Fitarki a asibin nan ma inaga sai da jami’an tsaro”.
Murmushi Lulu tai har yana iya jiyo sautinsa. Ta wawwaiga gefenta, tabbatar da babu kowa a kusa da ita cikin sake ƙasa da murya ta ce, “Karka damu zan tafi yanzu. Ka turo min address na wajen kawai kai dai”.
“Kin san mi kike faɗa kuwa. Taya zaki fita a gaɓar da wannan mara imanin ke nemanki ruwa a jallo. Ayanzu haka asibitin yake shirin tahowa dan ya samu tabbacin kina a ciki. Ga Uncle Yousuf nan zuwa shi da Daddy ma”.
“Ka kwantar da hankalinka zamu wuce plan E ne yanzu a kansa”.
“What! Plan E fa?. No no no Mawaddat. Bakya ganin halin da tsohuwar nan take ciki. Mu rushe plan E ma kwata-kwata bashi da amfani”.
“Shiko keda amfani musamman a wannan gaɓar Mr A. Dan babu abinda ya rage mana kuwa sai plan E ɗin. Dada ta riga taga video, shine ma dalilin kasancewar ta a wannan halin. A yanzu haka Grandpa da Uncles suna zaman meeting kuma nasan duk a kansa ne. So kaga abinda ya rage kawai mu ƙarasa sauran aikin. Dan haka yanzu zan saki….”
Da sauri ya ce, “Maw….” kafin ya ma ƙarasa sunan nata ta yanke wayar. Dan zuciyarta gaba ɗaya ta riga da ta gama kaiwa bango. Duk kiran da yake mata bata ɗaga ba. Cikin abinda baifi mintuna biyar ba ta gama sakin videon a ɓoyayyun shafukan data ɗauki tsawon lokaci tana raino da tara followers. Shafi ne da dama yake taka rawar gani akan harkar fyaɗe da shaye-shaye. Ta ginashi tun lokacin da su Dada suka saceta. Zuwa yanzu shafukan nada ɗunbin mabiya saboda abubuwan da ake posting a cikinsu. Sunasa kuma guda ɗaya ne a instegram, twitter, facebook, TikTok, da website. Sunan wanda ta saka, da abinda ta rubuta a saman video ɗin yasa cikin ƙanƙanin lokaci ya samu makallata masu ɗunbin yawa, kafin kace mi an fara shearing ɗinsa.
Yaron Alh. Sulaiman da suka kafa suka tsare a bakin asibiti na jiran fitowar Lulu ne ya fara cin karo da video ɗin, shima wani abokinsa ne ya tura masa yana tambayar ya duba wannan ba ogansa bane. Wani ihun tashin hankali ya fasa batare da ya farga ba. Har takai wanda ke ɗan wuwwucewa ta wajen suna kallonsa. Jiki na rawa ya shige mota. Kira ya dannama Alh. Sulaiman dake tsaka da yin online meeting shima a mota dan yana hanyarsa ta tahowa asibitin ya samu kira da ga Lagos. Sun buƙaci ya ajiye koma mi yake yi zasuyi online meeting na gaggawa. Hakan ya sashi samu waje yay parking hankali a tashe. Suna tsaka da tattaunawar akan batun kayansu ne dai kiran malami ya shigo masa. Bai yi niyar ɗagawa ba sai da yaga kira na biyar na sake shigo masa kuma duk da ga malamin ne. Yasan baya masa irin wannan kiran mafarautan, dan haka zuciyarsa ta bashi lallai akwai matsala. Dole yay excusing kansa ya ɗaga kiran.
“Oga ka duba na tura maka saƙo ta WhatsApp. Wlhy akwai matsala. Babbar matsala ma kuwa”.
Ba ƙaramin faɗuwa gaban Alh. Sulaiman yayi ba. Babu shiri ya shiga WhatsApp ɗinsa. Ai kawai sai ga mutumin waya na neman suɓuce masa. Duk da shi ya ga video ɗin amma tashin hankalinsa anan a ina malami ya samesa shi kuma? Ko amaryarsa da flash ɗin ke’a wajensa ce ta tura masa? Kai ina. Rashin samun gamsashiyar amsa ya sashi kiran malami. Muryarsa har harɗewa take wajen tambayarsa a ina ya samu video ɗin. Malami da gaba ɗaya yake a ruɗe ya ce, “Oga bama ni ba, a kowace waya zaka iya samunsa a yanzu. Dan an sake shi ne a wasu shafukan sada zumunta da ke a manyan apps da mutanenmu suka bama amanna. A yanzu haka wani abokina ne ya tura min wannan bayan na turo maka nima na shiga bincike wlhy tako ina videos ɗin trending sukeyi. Acikin abinda baifi minti arba’in ba miliyoyin mutane sun kalla”.
Karo na farko jikin Alh. Sulaiman ya shiga kakkarwa ta haƙiƙa. Bai gama dai-daita da wannan bala’in ba wani kiran ya shigo masa. Mai kula da ɓoyayyen Companyn sa ne na magunguna. Ruɗanin da yake ciki ya sashi ɗagawa batare da ya farga ba. Bai gama dai-daita wayar a kunnensa ba furucin Babban mai haɗa magunguna ɗin Companyn nasa ya daki kunnensa.
“Mun shiga uku Alhaji jami’an tsaro ne zagaye da dajin nan da Companyn nan. Gasu nan sun gama shiryawa da bindigu suna bamu umarnin mu miƙa kammu ta sauƙi kosu cinnama Company ɗin wuta. Yaya akayi haka Alhaji? Taya suka san da wannan wajen duk taka tsantsan ɗin da mukeyi na tsawon shekaru. Shike nan na mutu Alhaji kofa aure banyi ba balle na bar mai mun addu’a” ya ɓarke da wani irin kuka da ya nema fasa kwanyar Alhaji Sulaiman da gaba ɗaya ya gama jiƙewa da zufa. Ƙitt ya yanke kiran tare da tada mota a haukace. Wani kiran yaga yana shigowa, baida buƙatar duba wanene ma balle ya ɗaga. Kai tsaye gidansa ya nufa cikin wani irin mahaukacin gudu. Kaɗan ya rage ya take maigadinsa da ya gigita da horn. Baiyi parking na kirki ba ya fita cikin gudu-gudu daya firgita ma’aikatan gidan. Dan babu abinda babbar rigarsa keyi sai tashi sama bulummm-blummm-blummm. Yana gab da shiga falonsa ya nema yin wani uban tuntuɓe sai gashi ƙasa wanwar. Fuskarsa ta wani irin dunguruwa da ƙasa. Duk da azabar datake ratsa masa lips da goshe da kan hanci bai damu ba ya miƙe cikin ƙarfin hali. Sai ga jini na ɗiga yararara. Falon ya afka a ɗari uku da sittin, yana ajiye ƙafarsa ciki wayar da abokan huɗɗarsa ne kawai a ciki ta cigaba da ruri. Kamar zai fasa ihu ya ɗaga….
“Alhaji Sulaiman kayi takanka. Aiki ya buɗe wlhy yanzu haka an kame su Olu…..”
Wani irin kuka Alh. Sulaiman ya ɓarke da shi kawai tare da yakice babbar rigarsa da hular ya watsar. Sai kuma ya kwasa a guje zuwa cikin bedroom ɗinsa. (Gaskiya ka zare😂🤣😂🤣😂🤣😂🤣) Passport ɗin sa ya ɗakko, da gudu ya sake fitowa yana kai waya kunnensa. Malami yake kira yana ɗagawa ya ce masa ya siya musu ticket yanzun nan ta online nama kowacce ƙasane. Jirgin da zai tashi yanzu-yanzu dai yake buƙata. Yayi maza kuma su haɗu a airport.
Hankalin ma’aikatan gidan nashi ya tashi ganin gaba ɗaya kamar ya zare. A take sukai kiran Hajiya Turai suka sanar mata gida da babu lafiya. Dan sun gagara gane kan Alhaji gashi nan ya shigo a haukace, ya kuma fito ya shiga mota da alama sake fita zaiyi”. Kafin sukai ƙarshen wayar ma shi ya fice a gidan a haukace……
*_★UK★_*
Tun Smart da ke ganin komai na halin da Alh. Sulaiman ke ciki ta direct camara ɗin su yana dariya har al’amarin ya fara tada masa hankali. Jin da yay Alh. Sulaiman na shirya guduwa ya sashi saurin kiran Uncle Yousuf ya ce suyi report Immigrations office. Dan tabbas suka bari ya tsallake ƙasar yasha kenan. Dan a ƙasashen ƙetare yanada wanda zasu bashi kariya tunda bada kayan aka kamashi a hannu dumu-dumu ba. Cikin sauri Daddy ya aiwatar da hakan kuwa. Lokacin da Alh. Sulaiman da malami ke isowa airport har an fara shelar masu tafiya a jirgin Dubai su shirya. Sunyi farin ciki da samun hakan, dan Malami har ya siya musu ticket ɗin ta hanyar cuwa-cuwa ta hanyar wasu ruɓɓaɓun ma’aikatan da ke da alhakin hakan ta online. Restroom Alh. Sulaiman ya nufa domin canja kaya, yana fitowa har tuntuɓe ya nemayi wajen saurin nufar jirgin da har mutane sun fara shiga. Yana taɓa ƙofar ainahin inda hanyar zuwa wajen jirgin yake aka dakatar da shi duk da ya rufe fuska da facemask da glasses ga p-cap. Cikin masifa yake tambayar ba’asi. Kai tsaye ma’aikacin ya bashi amsa da yanzu-yanzu an tabbatar musu da karɓe lasisin fitarsa wata ƙasa. Sun samu saƙone kuma da ga immigrations office. Jiyay tamkar ya saki zawo a wando. Amma abinka da ɗan cocaine sai ya nema birkice musu har yana ƙoƙarin ture jami’in shi a dole zai wuce. Dai-dai nan aka sauke masa bindiga a saman kai tare da nuna masa handcuffs a kan fuska. A dake aka furta.
“You are under arrest Mr Garko..”
A wani irin hargitse ya juyo kunnensa na bada wani irin sautin tsuuuu!!! Kamar an doka masa guduma a kansa. Ido biyu yay da jami’an tsaro na ƴan sandan farin kaya wato DSS da na ainahin ƴan Sanda, dana immigrations sai na filin jirgin zagaye da shi kusan su hamsin. Kuma kowanne riƙe da bindiga. Gaba ɗaya airport ɗin tayi tsitttt baka ganin komai sai hansken wayoyin mutane dana ƴan jarida. Masu video nayi, masu hoto nayi, masu kallo nayi. Harda masu nunawa live a social media. Sai kawai ya rimtse idanunsa da sukai wani irin mahaukacin kaɗawa jazur, jijiyoyin kansa sun yi bala’in mimmiƙewa ruɗu-ruɗu. Bashi da zaɓin da ya wuce yin surrender kawai. Amma saboda ƙarfin hali da taurin zuciya irin na Tsule sai gashi da fakar ido ya hamɓari na gefensa bindigar hannunsa tai tsalle sama ya tare hannu ya cafe tare da ɗaurata saman kanta. A cikin abinda bai wuce sakan biyu ba hakan ta faru, shi adole sai ya tabbatar musu shi ɗin ƙwararren maharbi ne. Bindigar a saman kansa yana dariyar da tafi kuka ciwo da nunasu da hannu ɗaya ya ce, “Lusarai kawai. Da na miƙa kaina gareku wlhy Gara na kashe kaina. In ce dai shine ƙarshen abinda za’a iya min a duniya ko….”
“Karka aikata haka Mr Garko. Yin hakan kuskure ne ka miƙa kanka ga hukuma salin alin zaifi maka sauƙi”.
Shugaban NDLEA ne dake ƙarasowa yanzu ya faɗa daga inda yake tsaye. Wani banzan kallo Alhaji Sulaiman yay masa. Sai kuma ya kwashe da dariya yana ƙoƙarin ɗan kunamar bindigar. Tauuuuuu!!!! Kakejin sautin ya karaɗe airport ɗin da ya saka mutane fara kwasa a guje cikin ruɗewa da rikicewa…..
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣9️⃣
………Tana gama sakin videon da mintuna kaɗan Abdull na isowa asibitin shi da Asma’u. Da gudu tazo ta rungume Lulu cike da farin cikin ganinta. Basu wani ɓata lokaci ba suka shiga motar da Abdull ɗin ya tuƙo. Kai tsaye gidan da su Ammah ke zaune a yanzu kafin a kammala nasu da saura ƙiris suka nufa. Nan ɗin ma gida ne babba wadatacce da suke zaune babu takura. Duk zumuɗin ganin Ammahn da takeyi sai kuma ta ɓige da jin kunyarta. Ammah dake mata dariya ta rungumeta a jikinta tana mai farin cikin ganinta. Harga ALLAH ita tana jin Lulu a cikin ranta tamkar ƴar da ta haifa bawai suruka ba. Bata bari ta zauna ba sai da sukaje ta gaida Abba. Shima yayi farin cikin ganinta yana ta sanya mata albarka da mata ƙorafin rashin zuwa da AA bayan ya tambayeta jikin Dada. Duk da anan ɗin ma dai ya mata ƙorafin rashin faɗa musu da basuyi ba sai jiya suke sani. Haƙuri ta bama Abban da tabbatar masa suma basu sani ba sai da ga baya. Ta ɗan jima a wajen Abba suna hira sama-sama duk da ita duk a kunyace take kafin suka dawo ɗakin Ammah. Mama tayi ƙarfin halin zuwa mata sannu da zuwa kamar yanda taga aunty Amarya tayi. Bata nuna musu komai ba duk da dai taso taga idon Ummah, amma Asma’u ta sanar mata ai tana gidan yayanta ne sai an gama gini zata koma can da zama, sai dai Abba ya mata saki uku ma. Ko a jikin Lulu, sai ma zama data gyara tana shan kunun gyaɗa datace tana so Ammah da kanta ta dama mata. Dan a kallo ɗaya ta fahimci Lulu na ɗauke da ƙaramin ciki. Murnar kasancewa da su Ammah dan Maryam ma babu jimawa ta dawo daga makaranta ya mantar da ita wani batun Alh. Sulaiman. Sai dai tayi kiran Aunty Naja’atu ta tambayi ko Dada ta farka. Ta sanar mata bata farka ba ance sai bayan la’asar. Dan haka ta sake miƙe ƙafa har sai bayan la’asar ɗinne suka fito harda su Ammah da zasu je duba Dada. Sai a lokacin sukaji halin da garin Kanon ke a ciki. Abdull da Mubarak dake bibiyar komai suka shiga basu labari. Kwaɓarsu Ammah ta shiga ƙoƙarin fara yi wai saboda Lulu, amma sai sukaji lulun na ƴar dariya da faɗin, “Ammah barsu su bamu musha. Indai wannan ne baida maraba da wanda ban haɗa komai da shi ba a duniyar nan, dan inda akwai wanda ya tsanesa to nice farko kuwa.”
Shiru kowa ya kasa cewa komai a motar har suka iso asibitin dan furucin Lulun ya girgiza zukatansu…..
_________★
Ba jama’ar gari ba, hatta jami’an tsaron duk sun ɗauka Alh. Sulaiman ya kashe kansa ne. Hatta Smart da ke kallon komai ta can wani irin rumtse idanu yay da dunƙule hannaye ya kaima iska naushi da faɗin, “Ohhhh Shiittttt!!!!”.
Wahalalliyar ƙarar da Alh. Sulaiman ya sakice ta saka kowa ɗagowa da sauri. Dai-dai Alhaji Sulaiman na kaiwa ƙasa durƙushe akan gwiyawunsa bindigar hannunsa na faɗuwa ƙasa itama ya dafe hannun damarsa dana haggu dai-dai inda ƙwararrren maharbin jami’in ya sakar masa bullet. Kowa kallonsa ya maida akan jami’in, shiko ko’a jikinsa sai ma hura bakin bindigarsa da yay da baki ya turata cikin aljihun wandonsa yana ƙarasowa gaban Tsule. Wani irin fisgar hannuwan nasa duk biyu yay zuwa baya batare daya damu da jinin dake ɓulala a hannun Alh. Sulaiman ɗin da bullet ya ratsa ba balle jin tausayin maɗoɗowar azabar da yake yi ya saka masa handcuffs. Sai a lokacin mutane suka farga da ashe bai kashe kan nasa ba jam’in yay nasarar harbinsa a hannun bindigar ta faɗi.
Cikin ƙanƙanin lokaci zufa ta gama jiƙe Alh. Sulaiman. A haka aka taso ƙeyarsa zuwa wajen airport ɗin yayi wujiga-wujiga. Da ƴan uwansa ya fara tozali tsaye reras su huɗu mahaifinsu a tsakkiya cikon na biyar. Kallo ɗaya dayay musu bai sake marmarin ƙarawa ba saboda irin wutar bala’in da ya hanga a fuskokin nasu musamman ma autansu na maza dake wani irin huci kamar kumurcin maciji Uncle Taheer. A karo na farko yaji wasu irin hawaye sun sakko masa masu zafi da ɗaci. Babu zato babu tsammani yaji saukar wani irin gigitaccen mari maisa a gano ƙyallin kabari har saida ya durƙushe ƙasa. Bai gama dawowa a hayyacinsa ba aka sake sauke masa wani. Ba kowa bane da wannan aikin face auta da Uncle Amin. Har sai da sauran ƴan uwansa Uncle Muneer da Uncle Khamil suka rirriƙesu. A hankali Baba Garko ya ƙaraso gabansa hannunsa riƙe da ƙyaƙyƙyawar sandarsa ya zuba masa idanu na wasu sakkani. Sai kuma cikin ƙarfin hali ya saki murmushi mai ciwo. Cike da dattakon nan nasa yasa sandarsa ya ɗago haɓar Alh. Sulaiman da bai gama dawowa daga gigitar marin da yasha hannun ƙannesa na uku dana huɗu ba. Muryarsa da ɗaci sosai yace, “Sulaiman bazan maka baki ba. Sai dai ina baƙin ciki da takaicin saka maka suna mai daraja da kima irin wannan. Sannan ina jin raɗaɗin kasancewar ka jinina. Sai dai bazanma UBANGIJI butulci ba, domin ya bani huɗu gasu nan duk na ƙwarai, tare da biyu mata da basa raye duk da kaine kai sanadin mutuwar Sultana. Sulaiman kai ba mutum bane shaiɗani ne, dabbane tunda har zaka iya haikema ƙanwarka ƴar shekara tara kacal da lafiya bata isa ba. Kaiconka Sulaiman ka tabbatar asararre a wannan duniyar wlhy. Gashi nan kazo a banza zaka koma a wofi dan bana maka fatan shiriya harka koma ga ALLAH. Yau ina kuɗin daka tara ta hanyar haramun ɗin? Ina damar da kake ganin kanada ita ta lafiya da rayuwa da dukiya? Ka lalata dubban al’umma ta hanyar miyagun kwayoyi, kasa iyaye da yawa kuka! Kasa mataye da yawa kuka! Kasa mazaje da yawa kuka! Ina zaka da hakkin waɗan nan bayin ALLAH koda basu furta maka ALLAH ya isa ba. Kaiconka Sulaiman, wlhy bana fatan wani ya yafe maka akan wannan al’amarin koda mutum ɗaya ne. Kaje in dai duniya ce gaka nan a cikin tarkonta, ka gama wahala a cikinta kaje ka fiskanci hukuncin UBANGIJI kuma. Da ga yanzu na haramta maka sake amfani da sunana kona zuri’ata har bada”. Daga haka ya juya yana sharar hawaye. Yaransa dake bin Sulaiman da mummunan kallo suka take masa baya.
Wani irin durƙushewa Alh. Sulaiman yayi a wajen ya ɓarke da kuka. Dan kalaman makaifin nasu sunyi masifar shigarsa shiga mai tsanani da ƙarfi a cikin jini da ɓarko ta yanda baiyi zato ko tsammani ba. Da ƙyar jami’an tsaron suka iya ɗagashi aka jefa a cikin mota….
*_3 DAYS LATER_*
A yanzu kam babu wani latest topic dake yawo a media da gari sama dana Alh. Sulaiman. Hatta maganganun da Baba Garko ya faɗa masa da marin da ƙannensa sukai masa sai yawo suke a social media. Hakama ɓoyayyen Companyn sa na magunguna sai da aka gayyaci ƴan jaridu sannan akai masa filla-filla. Baba Garko da ƴan uwansa sunje har Companyn suma. Sosai hankalinsu ya sake tashi saboda ganin ɗunbin aika-aikar da jinin nasu ya jima yanayi batare da sun farga ba. Harda jarirai a wajen da ake gwada magani a jikinsu kafin a fitar, wasu sukan mutu wasu su kamu da ciwuka al’amarin zattashin hankali dai. Ƴaƴansa kam kuka har suna rasa hawaye. Dan biyu da ga ciki harda saki mazajensu sukai musu.
Duk yanda Baba Garko ke ƙoƙarin danne komai ya cigaba da zama ba komai ba hakan ya gagara. Dan kuwa dai sai da takaisa kwanciya a gadon asibiti. Yayinda aka samu ita kuma Dada ta maro. Sai dai bata iya dogon magana sai kuka da jama Sulaiman kalaman ALLAH ya isa da faɗin, “Nayi dana sani ni Hajarah, dama Mawaddat tasha faɗa min Sulaiman na lalata yaran masu aiki kuma nima na sani amma son zuciya da son ƴaƴa ya hanani ɗaukar makaki sai da akaima Sultana fyaɗe. Ashe na rigada na makara tun a wancan lokacin, ashe shine ya wulakanta min mutuncin yarinya ya halaka min ita. Yarinyar da ko cikakkiyar lafiya bata da shi. Kaicona ni Hajara kaicona da irin son zuciyata. Gashi nan takaini ta baroni a gaɓar da bazan iya komai ba na dawo da baya balle na gyara. Wane irin abin kunya ne wannan da tozarci. ALLAH ya tsine maka Sulaiman. ALLAH ya ƙuntata rayuwarka tun daga nan duniya. Wlhy bazan yafe maka ba. Inama ɓarin cikinka nayi ko mutuwa naima gaba ɗaya a lokacin haihuwarka. Dama kin cemin zanyi nadama mara amfani idan ban gyara ba, kin faɗamin banji ba Mawaddat,, ban saurareki ba, da ace na saurareki da banga wannan mummunar ranar ba a rayuwata. Inama na mutu kafin zuwan wannan ranar. ALLAH ya isa Sulaiman…..” ta sake fashewa da kuka. Lallashinta aketayi akan ta daina tsine masa da muguwar addu’ar nan. Amma ina Dada idonta a rufe yake. Babu abinda take hangowa sai Sultana kwance cikin jini, yarinyar da har aka kaita makwancinta jini bai daina fita a jikinta ba. Haka aka sakata a kabarinta likafaninta duk jini.
Lokacin da Lulu dake kwana a wajen Ammah yanzu ta shigo Dada ta riƙota jikinta tana kuka. Itama sai Lulun ta kama kuka. Da ƙyar Uncle Khamil ya janye Lulu da ga jikin Dada saboda aman jinin data fara. Dama Doctor ya sanar musu zuciyarta ta taɓu sosai sai abinda ALLAH yayi kawai. Hankalin kowa ya sake tashi, dan Baba Garko ma hanawa akai a faɗa masa……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣0️⃣
……..Sai da suka tabbatar ya gama jigata da bullet ɗin da ke jikinsa sannan suka cire masa. Washe gari suka bisa da duka na hauka wanda ya kaisa harda karaya a ƙafa, suma kam yayita babu adadi suna farfaɗo da shi. Duk wanda yaga yanda ake wajiga rayuwar Sulaiman zai tabbatar da al’amarin da biyu ne. Inda ma aka ɓoyesa kawai tashin hankali ne. Dan da ƙyar Daddy da Lulu ta matsawa da son ganin Alh. Sulaiman ɗin sukaje aka barsu suka ganshi, ya samu wannan alfarmar ne kawai saboda taimakon da ya bama jami’an tsaro wajen cafke su Alh. Sulaiman ɗin. Daƙyar Alh. Sulaiman ya iya ɗaga ido ya kalla Daddy da Lulu data juye masa tamkar mahaifiyarta, saboda duka ya taɓa masa ido ɗaya. “Miya kawoka wajena?!”.
Ya faɗa da ƙyar muryarsa na karkarwa. Iska Daddy ya firzar yana mai ƙoƙarin maida hawayen da suka cika masa ido. Dan ganin yanda akaima Sulaiman ɗin raga-raga a kwana biyu kacal ya ɗaga masa hankali. Da ƙyar ya iya danne rawar lips ɗinsa ya furta, “Nazo ne na tabbatar maka wasan ya ƙare Sulaiman. Dama irin wannan ranar nake guje maka a baya amma ka kasa raurarena da fahimtata sam. Ka ɗauki tsawon shekaru kana tsula tsiyarka amma ka duba cikin abinda bai wuce awanni arba’in da shida ba ka koma tamkar bakai ba. Wannan fa kamun mutane ƴan uwanka kenan. Inaga kamun UBANGIJI kuma Sulaiman. Duk wahalar da kasha rani da damuna da sanyi, wahalar yawon ƙasashe domin tara dukiya kawai kallo a inda ka kasance yanzu. Talakan da bai taɓa riƙe dubu hamsin ba ya fika. Babu abinda yafi neman halak komai ƙanƙantarta sauƙi a wannan rayuwar. Koba komai zaka rayu cikin kwanciyar hankali ka kuma mutu cikin mutuntawar UBANGIJI. Mutane su ɗauki gawarka da girmamawa, a taya iyalinka kuka da jajantawa a tausaya musu. Amma ta irin hanyar da kuke bi fa? Zaka kasance cikin ALLAH wadai wa zuri’ar ka da al’ummar gari, kabar iyalinka da hantara wanda ma bai kai ya takasu ba ya taka su. Maimakon addu’a ga mutane sai ALLAH wadarai ke fita a bakunansu. Duk inda mutum ya buɗe a yanar gizo ciki da wajen Nigeria zancenku ne. Miye amfanin ɗaukakar ALLAH ya tsine irin wannan. Kasaka iyayenka a wani hali da iyalanka. Iyayenka mutanen kirki ne Sulaiman musamman mahaifinka, mutumne mai daraja da kima a wajen mutane, a duk inda ka zagaya alkairinsa ke fita daga bakunan mutane. Amma yau gashi kasa al’umma na ambatar sunanka a matsayin jininsa. Albasa batai halin ruwa ba Sulaiman……”
Kuka ya sarƙe Daddy mai cin zuciya. A mamakinsu sai ga Sulaiman na hawaye shima. “Maganganunka dukansu gaskiya ne Isma’il. Tabbas mun kasance masu son zuciya a rayuwarmu. Burin tara dukiya duk da wasunmu mun tashi a gidan dukiyar. Burin zama wasu abu a duniya batare da muna tuna muna mutuwa ba. Da’ace na saurareka tun a wancan lokacin Isma’il da ba’a kai wannan gaɓar ba. Yau gani a matsayin wanda ya rasa komai. Babu iyayen da suka sha wahalar haihuwata da bani tarbiyya da ilimi. Babu matan dana ɓata lokaci wajen neman dukiyar dan na birge su, babu ƴaƴan da nake zumuɗin tarawa domin a kirasu ƴaƴan wane. Babu ƙarfin da nake kai duk wanda ya bijiremin ƙasa. Babu ƙarfin da nake tunanin wataran zan iya sarrafa ƙasar dama wasu ƙasashe a hannuna. Komai ya ƙare Isma’il, komai ya kufce a gaɓar da nake gab da cimma nasara mara amfani. Komai ya tafi kamar bai taɓa zuwa ba…..” kuka ya sarƙe sa.
“Dan ma bakaji irin tsinuwar da uwarka ke maka bane ba! Da nadamar haihuwarka”. Lulu ta faɗa kanta tsaye babu alamar tausayinsa ko ɗigo a ranta. Dan itafa in dai ka kasance kayi fyaɗe to babu abinda zaisa taji tausayinka dan ta ganka a wani hali. Cikin tashin hankali Alh. Sulaiman ya ɗago yana kallonta. Ta wani ƙyaɓe baki da cigaba da faɗin, “Ai yanzu bakaga komai ba ma. Dan an gama wasanne saura yaƙin. Shi kuma yaƙin yanzunne aka fara shaiɗani. Wai kaine kake kuka nadama a cikin kwana biyu kacal. Ƙaryane ma na yarda da hakan makiri. Idan ma tunaninka Daddy na zai taimakeka ka fito ne ka cire hakan a ranka dan ka shiga kenan, kabarinka ma anan zasu gina maka shi su bizneka babu wanka babu sallar gawa. Wannan da kake gani yafi ƙarfinka kamar yanda ya faɗa maka tun farko, bama shi ba, mu dake ƙasa da shi munfi ƙarfinka dan gashi a ƙanƙanin lokaci mun sabauta rayuwarka tamkar ma ba’a taɓa yinka ba balle iyawarka. Nasan dai bazaka manta da wannan fuskarba ai”. Ta faɗa tana juya masa wayarta. Smart ne ya bayyana AA zaune a saman cinyarsa. Fuskarsa ɗauke da murmushi ya ɗaga ma Alh. Sulaiman hannu da faɗin, “Hy ƙwaro”. Sai kuma ya saki ƴar dariya yana ɗage gira sama ganin yanda Alh. Sulaiman ɗin ya saki baki da hanci yana kallonsa. Nunasa ya shigayi wasu irin zafafan hawaye na rige-rigen sakko masa. Lips ɗinsa na rawa sai dai ya gagara cewa komai.
“Kwantar da hankalinka ai basai kace komai ba zan ƙarasa maka. *_Aliyu Mika’il Idris Mawashi_* ne dai naka. Yaron nan daka tura aiki jiƙamshi family. Idan baka manta ba na faɗa maka kada ka ƙulla wasa dani zan iya kaika ƙasa. Amma sai ka gagara ganewa saboda kana kallona yaro ƙarami ɗan talakawa da zaka iya hurewa tamkar silin gashin kanka a lokacin da kaso. Kayi kuskure Sulaiman dan ba’a raina maƙiyi koda na jinjirin sauro ne. Kamar yanda na faɗa maka ni kurari baya razanani hakanne, sai ma ƙaimi da yake ƙaramin. Da’ace baka kalleni a ba komai ba maybe da kaci nasarar tsallakewa da ga tarkona. Sai dai kash girman kanka da ɗaukar kanka sama da kowa yasa kai sake ɗan zaki ya girma yay gawurtar da ya wuce da saninka. Ka sani ni bani da wata matsala da kai dan babu abinda ya taɓa haɗamu kafin saninka. Kawai na ƙarasa aikin family na na biyu ne. Wato aikin surukina da surukata da kuma matata, dan duk wanda ya taɓasu kowaye shi bazan taɓa ƙyalesa ba saboda sunansu AHALINA suma a yanzu. Ni kuma ba’a taɓamin AHALI a zauna lafiya, sai nayi kaca-kaca da rayuwar mutum ta inda bai zata ko tsammani ba. Kamar dai yanda a yanzu muka shafe tarihinka da babinka. Ka sanar musu su cire maka camara ɗin dake gefen kunnenka dan aikina ya ƙare, bana buƙatar cigaba da ganin yanda kake cin ubanka a hannunsu bye bye Solomon”.
Dariya Solomon daya kirashi ya bama Lulu. Ta shiga ƙyalƙyalawa kuwa. Dai-dai nan jami’in ya shigo yake sanar musu lokaci ya cika. Ko’a jikin Lulu ta miƙe tana ɗagama Sulaiman yatsu biyu. Sai kawai ya bita da kallo wasu irin hawaye masu zafi na silalo masa. Dan babu abinda yake gani a tattare da ita sai mahaifiyarta. Gaba ɗaya ta juye ta koma masa Mawaddat ƙanwarsa. Duk da dama tana kama da ita mai tsananin gaske. Jiki a saɓule shima Daddy ya tashi ya fito.
Koda suka tafi a mota kasa cema Lulu komai yay sai da sukaje gida yace ta biyosa falonsa……
Wannan zuwa na Daddy ya tsayama Sulaiman a rai matuƙa. Zuciyarsa bata nema bugawa ba sai da aka cire camara ɗin da Smart yace a gefen kunnensa. Wani irin raɗaɗi yake ji a ransa da mamakin ta ya akai camara a jikinsa bai sani ba, har tsawon wane lokaci yaran nan suka ɗauka suna wasa da hankalinsa batare da ya taɓa farga ba. Sai yanzu ya gane Smart ne *_AMM_* da ya dinga turo masa saƙwanni. Tabbas yaron yayi gaskiya, ya ɗaukesa a bakomai ba, amma gashi ya zame masa komai. Ya kaisa ƙasa a lokacin da bai zato ko tsammani ba, ashe abinda suke zargin wani babban mai faɗa aji ke musu shine ke aikata musu shi. Yaron da basu taɓa kawowa a hasashen su ba. Shi baima taɓa kallonsa a jerin maƙiyan da zasu iya juya rayuwarsa haka ba. Ranar yaci kuka mai suna kuka da har sai da ya rasa hawaye. A rana ta uku aka ɗaukesa da ga Kano gaba ɗaya zuwa Lagos. A rayuwarsa bai taɓa sanin akwai azabar rayuwa irin wannan ba a duniya. Duk da yasan shi mugune, sun kuma kashe mutane da dama a dalilin harkar ƙwayar da sukeyi idan suka bijire musu. Amma wannan ɗin na musamman ne. Duk taurin zuciya da taurin kai irin na Alh. Sulaiman a wannan gaɓar sai gashi yana hawaye, shi kansa yasan anzo dai-dai wajen kuma. A randa aka isa da shi Lagos wahalar da yaci bai ma san ya fara kiran sunan Dada da Baba Garko ba akan suzo su taimakesa ya tuba, har Hajiya Turai da Tajuddeen da sauran ƴaƴansu sai da suka sha kira. Wannan itace nadama mara amfani, domin kuwa bakin uwa shine ke tasiri akansa tare da haƙƙokin mutane dana ƴaƴansu da suka zama sanadin lalatama rayuwa ta hanyoyi da yawa, gashi nan a kwanaki uku kacal rayuwarsa ta sauya a yanda ko maƙiyinsa ya gansa dolene ya tausaya masa, dan a yau ma sai da suka sake masa karaya biyu a hannu ɗaya. Bai san sanda azaba ta sakashi fara lissafo abokan huɗɗarsa ba. Wanda dama tunda aka kamashi hankulansu a tashe suke matuƙa suma, sau faman kai gwauro da mari sukeyi akan al’amarin shiyyasa ma aka ɓoye Alh. Sulaiman ɗin ashe……….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣1️⃣
……An cigaba da kame-kame a ƙasar mai ban tashin hankali. Inda harda sunan wani tsohon shugaban ƙasa, da wasu manyan ƴan siyasa a gwamnoni da ƴan majalisu ma dake ci a yanzu ya fito, sunayen manya-manyan ƴan kasuwar da ba’a taɓa zato da tsammani ba. Tare da manyan ma’aikatan gwamnati da tsabar yanda ake kallonsu iyayen ƙasa ake kiransu. Al’amari yakai intahar da mai gyarashi sai dai UBANGIJI. A cikin abinda baifi awanni a shirin da huɗu ba na cikar kwanakin Sulaiman a hannun hukuma sojoji suka sauke shugaban ƙasa tare da wasu gwamnoni. Hankalin mutane ya tashi matuƙa da tunanin ko juyin mulki ne, sai gashi bayan cikar wata a wa ashirin da huɗun an maye gurbin shuwagabannin da mataimakansu amma an maida shugaban ƙasar shima….
_____★
An wuce da Dada da Baba Garko zuwa ƙetare domin duba lafiyarsu. Hakan yasa Lulu shiryawa itama ta koma wajen mijinta bisa umarnin su Daddy. Taso ganin Ummah itama amma hakan bai faru ba saboda kai-kawon da tayi duk bata jin daɗin jikinta. Smart da kansa yaje tarbarta airport shi da ɗansa. Ta rungumesu su duka cikin ƙarfin hali da jin kewarsu duk da dudu kwananta tara ne kacal. Suna isa gida ta zube kwance a falo, hakan yasa kowa ya fahimci bata jin daɗin jikinta. Kiran Ammah da ya shigoma Smart da ke kallonta ne ya hanashi magana. Sai da ta katse ya kirata dan haka yake musu duk wanda ya kirashi koda a yaran gidansu ne. Bayan ya gaisheta da girmamawa take tambayar ƴan tafiya sun iso lafiya. Cikin ɗan damuwa yace, “Gata nan duk a galabaice muna shigowa ta zube a falo.”
“Ya salam, ai kuma dai kunyi ganganci ne. Dan ma ALLAH ya bata ƙarfin hali ne kawai. Amma a halin da take ciki ai ba kowa zai iya ɗaukar wannan kai-kawon ba da hayaniyar da aka sha. Sai kuyi ƙoƙari ku tafi asibiti dan a tabbatar da lafiyar abinda ke jikin nata da ita kanta”.
Cike da mamaki Smart da ke kallon Lulu ya ce, “Ammah abinda ke cikinta kuma? Wani abu tace miki yana damunta?”.
Cikin murmushi mai sauti Ammah ta ce, “Aiba saita faɗamin ba Babana. Duk wanda ya kalli Mawaddat ai yasan akwai ciki a jikinta”.
“Ciki fa Ammah?”.
“A’a kaini tsaya, wai ku baku san da cikin ba ne ko mi?”.
“Wlhy Ammah ni ban san tana da ciki ba. Itama kuma na tabbata bata san da shi ɗin ba”.
“Kai nikam yau naga sakarkarun yara. Yanzu ita Bilkisun dake tare da ku ga wannan tsohuwar ace suma duk basu lura ba. Aiko wannan cikin in bai kai wata huɗu ba ma to gab yake da kaiwa. Dan da alama ma babu jimawa da zuwanta nan ALLAH ya bada shi. Sai kuyi ƙoƙari dai kuje asibiti to”.
A sanyaye yace, “To Ammah insha ALLAHU”.
Yana yanke wayar Lulu ta miƙe cikin ƙarfin hali zuwa bedroom. Dan wanka kawai take sonyi. Da kallo suka bita su duka. Iya Tabawa ce ta katsesu da ƴar dariyar ta. A tare duk suka juyo suna kallonta. Tace, “Ai tun watan daya gabata na fahimci uwar ɗakina nada shigar ciki. Nayi shiru ne dai kawai saboda dambarwar da naji anayi”.
Dariya aunty Bilkisu tayi sosai tana kallon Smart daya rasa abin cewa. “Ka gani kunata faman fitina ashe ma ALLAH ya bada abinda ake ma rigimar. Nima sai gab da zata tafin nan na fahimta sai dai zuciyata bata tabbatar ba shiyyasa bance komai ba. Ashe Iya Tabawa ta mana na manya ne ma ita. ALLAH ya raba lafiya, ya bata lafiya ita kuma”.
A hankali ya amsa da Amin yana sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ya miƙe yabi bayanta zuwa bedroom ɗin. Ya samu tana wanka, dan haka ya zauna a bakin gado yana zaman jiran fitowarta. Babu jimawa ko sai gata ta fito tana faman dafe kai. Miƙewa yay ya riƙota ganin kamar tana tangaɗi. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Miya faru kuma?”.
“Ina ganin jiri” ta bashi amsa a hankali. Kwantar da ita yay a saman gado ya rungumeta a jikinsa yana mai sauke tagwayen ajiyar zuciya. Idanunsa a lumshe yana shafa mata kai ya ce, “Dama kin san kina da ciki amma kika kasa sanar min?”.
Kanta ta girgiza masa a hankali da faɗin, “Wlhy ban sani ba. Duk da ina jin canji a jikina ba a yanda na saba ba na ɗauka kawai yanayi ne dan lokacin cikin AA ma sai da ya kai wata kusan huɗun na sani bayan ma anyi yunƙurin zubar da shi”.
Sake ƙanƙameta yay a jikinsa yana mai jin wani irin farin ciki mara misalin kwatance. Sosai yake son ƴaƴa a rayuwarsa. Kodan ta tashi cikin yawa ne a gidansu shiyyasa oho. A hankali ya shiga bata sumba yana mai sanya mata albarka. Ita dai riƙe kukanta kawai takeyi amma ita tasan mi take ji. Bawai bata farin ciki bane ba. Tana jin tsorone kawai dan ita kaɗai tasan irin wahalar da tasha a lokacin haihuwar AA da sanda cikinta ya tsufa. Sai dai a yanzu tana tsoron nunawa kuma ta takaloma kanta bala’insa. Haka ta cigaba da shanyewa da barma ranta kawai tunda dai mai afkuwa ta afku, sai dai tana mamakin ciki a jikin mace nayan tayi planing, gaskiya mutumin nan maye ne, itakam taga takanta kenan. Shi da kansa ya shiryata yana ta dai ƙoƙarin danne dariyarsa, dan daya tuna abinda tayi kuma ga cikin da take gudu sai yaji dariya na taso masa, haka dai ya daure ya kimtsata sannan ya fita ya kawo mata kunun gyaɗar da tace tana so yanata fan murmushi sai dai baice komai ba duk da bakinsa fal yake da zance. Kaɗan ta sha tace ta ƙoshi, daya matsa ma sai ta fara yunƙurin amai. Dole ya ƙyaleta suka wuce asibiti. An dubata tare da tabbatar musu baby na cikin ƙoshin lafiya. Gajiya ne kawai yay mata yawa, dan haka sukace taje ta samu hutu sosai a gida dan tana buƙatar bedrest. Sai magunguna da suka bata na ƙarin kuzari da ranakun da zata dinga zuwa ana duba lafiyarta suka kuma cire mata abinda ta sakama jikinta kamar yanda ta buƙata, dan bataga amfaninsa ba kuma. A haka suka kwaso suka dawo gida Smart na kwasar dariya dan a wannan gaɓar dai ya gagara daurewa. Itako sai kawai ta sakar masa kuka dan ta gane abinda yakema dariyar. (Mugu ɗan masa kenan😂😂)
A ranar dai duk ƙwaɗayinsa dole ya haɗiyesa saboda kwana tai babu lafiya, sai amai da take faman yi ko ruwa ta sha. Washe gari dole suka sake komawa asibitin. Kwantar da su sukayi suma dole. Gashi washe gari yana da wasa mai zafin gaske dan gab suke da kaiwa ƙarshen primier link. Alhmdllh Dan yana taka rawar gani sosai ga kuma team ɗinsu na gaba da kaiwa zagayen ƙarshe. Babu yanda zai yi dole ya shirya ya koma ya barta da su aunty Bilkisu….
★Satin Lulu uku da dawowa aunty Bilkisu ta fara shirin komawa Nigeria. Alhmdllh taji sauƙi sosai sai fatan lafiya mai ɗorewa. Shatara ta arziƙi Lulu da Smart suka shirya mata. Haka ta wuce suna jin kewarta tana jin nasu dan Lulu harda hawayenta. Sai da Smart ya dinga lallashinta akan ta kwantar da hankalinta ba sun kusa tafiya bikin Maryam ba. Idan zasu dawo da Ammah zasu dawo in sha ALLAH. Hakan ya sakata jin farin ciki sosai.
Lulu ta cigaba da rainon cikin ta cike da kulawar mijinta da Iya Tabawa da ta zame mata tamkar uwa. A haka su Aunty Saliha sukazo hutu UK, kuma anan London sukai masauki kamar yanda Lulu taita naci. Sosai ta kasance cikin farin ciki mara misali. Balle ga ɗan lelenta Deen kuma da ya ƙara girma. Cikin jikinta daya fito sosai bai hanata yin hidima da su ba, dan kusan a gidan suke yini ma. Sai dare su koma masaukinsu. Wani lokacin kuma ita taje can.
Su Smart sun kai zagayen ƙarshe tare da ɗaukar kofi. Yayinda Smart ya taka rawar gani da sunansa keta sake zama abin ambato a zuciyar masoyansa. Ga ƴammata tako ina sun sakkoshi gaba. Sai dai shi ko kallo basu ishesa ba, dan yace ya rufe da ga Final Choice babu wata kuma. Kammala wasansu ya sashi fara musu shirin tafiya Nigeria dan ya samu hutu mai ɗan yawa. Ga kuma bikin Maryam da aketa shirye-shirye dan dama saboda shi aka ɗan ɗaga ƙafa….
*_NIGERIA_*
A Najeriyar ma abubuwa da yawa ne suka faffaru. Su Ammah sun koma gidansu da Smart ya gyara. An canja masa tsari mai birgewa da ɗaukar hankali. Yayinda Abba yace Ummah bazata dawo masa gida ba tunda ya saketa. Sai da aka taru a kansa anata bashi haƙuri akan tazo tai zaman ƴaƴanta. Cikin ƴan roƙo harda Smart. Da ga ƙarshe dai da ƙyar ya amince. Kasancewar itama da nata sashen ta dawo. Sai dai lokacin da zasu shigo gidan bata ma san ta ɓarke da wani irin kuka mai cin zuciya ba. Yanzu nan Aliyu ne ya gina musu wannan gidan. Duk faɗi tashinta dai ya tashi a banza a wofi an kai inda dai bata son kenan. Ranar kwana tayi tana kuka ita kaɗai a ɗaki. Wani tashin hankali kuma washe gari suka tashi da gobara a shagunan Salim. Komai ya ƙone ko tsinke ba’a fita da shi ba. Ana cikin wannan tashin hankalin ƴarta Hannatu ta dawo gida wai mijinta ya saketa. Gaba ɗaya Umma ta sake hargitsewa jiki ya koma ɗanye sharaf. Sai da aka kira Smart ana faɗa masa ne ya saka aka kaita asibiti. Satin ta ɗaya aka sallamonta. Gaba ɗaya Salim ya koma kamar zararre. Sai kuka yake yana jama Umma ALLAH ya isa akan itace ta ja masa. Ai dama nakan tudu ya faɗa duk bala’in data ƙulla akan Smart sai ya dawo kansu. Gashi nan kuwa. Ta cucesu ta zalunce su bazasu yafe ba. Ranar da matar Salim ta gudu da ƴaƴansa bayan ta saida gidan da shi ya kaɗai ya rage masa ai kaɗan ya rage a ɗaureshi a turu saboda tsabar zaucewa. Umma ta dinga kuka dan dama dai Salim ɗin ne abin tinƙahonta………..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣2️⃣
…….A ɓangaren Garko family ma dai ALLAH ya bama Dada da Baba Garko lafiya har sun dawo gida Nigeria. Sai dai Dada ƙarfin hali kawai take. Gaba ɗaya ta zama wata shiru-shiru. Sai da kaga ta tasa hoton Maman Mawaddat da na Sultana gaba tana kuka. A yanzu Baba Garko kan zauna ya lallasheta da mata nasiha. Hakama amaryarta takan ƙyautata mata duk dan dai ta kwantar da hankalinta, haka ma ƴaƴanta basa gajiyawa wajen tattalinta saboda an tabbatar musu zuciyarta idan har ta buga shike nan kuma. Dan haka kowa baya wasa da al’amarinta. Lulu kanta ba’a barta a baya ba wajen lallashin Dadan. Dan tana kallonta tamkar Mawaddat ɗin ta ne data rasa. Akoda yaushe cikin yin video call suke da ita….
__________★
Shirye-shiryen bikin Maryam ya kankama sosai, dan takowane ɓangare shiri kawai akeyi. Ana saura sati guda ɗaurin aure Smart da iyalinsa suka iso gida Nigeria. Ƙasar da yay kewa. Tarba ya samu maiban mamaki da ga al’ummar ƙasar tasa da ƴan uwa da abokan arziƙi. Dan da ƙyar suka iya baro airport sai da taimakon jami’an tsaro. Yayinda ya samu rakkiyar masoya har gida. Anan ma ya samu yaran anguwa da iyaye suna jiransa. Sai ga Smart na hawaye dan farin ciki. Ya tabbatar da mutane rahama ne. Duk wanda yace maka yana sonka da ƙaunarka ya gama maka komai a rayuwa. (Ya ALLAH ka barmu da masoyanmu. Duk wanda ya somu dominka ya rabbi shima ka soshi shi da zuri’arsa baki ɗaya. ❤️❤️❤️😘 wannan nakune masoyan alkairi 🙏).
Anan ɗin ma dai da ƙyar ya samu suka shiga gida saboda yanayin Lulu. Dan cikinta yayi girma sosai wannan karon fiye dana AA. Ga kuma kullum cikin laulayi take dan tunda ya fara tsufa bata da wani ishashen lafiya. Duk da dama dai haka taketa fama tun da cikin ya shiga watanni biyar. Babu kunya yau kam Smart ya rungume Ammah da Abbah a gaban jama’ar gidansu. Ya kuma rungume ƙannensa su Mubarak da yasan suna matuƙar kaunarsa. Kannensa mata nata kawo masa gaisuwar girmamawa harma da wanda suka girmesa kamar wani sarki. Tunda Ummah ta leƙo sau ɗaya ta gansa bata sake maimaitawa ba, ɗaki ta shige tana sakin wani irin kuka mai ƙona zuciya. Smart ya koma kamar wani baƙin bature. Ko makaho ya laluba yasan kuɗi da jin daɗin rayuwa da ɗaukaka sun zauna sai dai fatan gamawa da rayuwa lafiya.
Shiko sanin bata da isashiyar lafiya har ɗaki yaje ya gaisheta tare da duk sauran matan Abba har aunty Amarya. Ita kanta Mama a ruɗe take, kawai dai tana ƙoƙarin dannewa ne kar ai mata irin kallon da akema Umma. Dan ƙamshin Smart kawai rikita zuciya yake. Saboda kowa ya gama sanin hankalin Ummah fa a tashe yake. Wasu a cikin yaranta har abun nata na basu kunya.
Bayan yaci ya sha daga girkin mahaifiyarsa data musu girki da kanta dan Lulu bata iya cin komai sai kunun gyaɗa. Shi kaɗai taima sha na hauka dan motsi kaɗan taji yunwa yanzu. AA na hannun iyayensa wannan ya ɗauka ya ba wancan haka aketayi. Yaron birgesu yake gashi fes kamar ka lashe, komai na ubansa bai bari ba. Zuwa yanzu ya ɗan fara magana sai dai ba gane abinda yake nufi akeyiba ma sosai. Kwanciya Lulu tayi danta hutama ranta. Yayinda su Ammah da Smart suka buɗe shafin hira dan Gwaggo Sa’adah na gidan da su aunty Bilkisu da Hawwah. Daga baya sai ga Abba shima ya shigo duk da su Smart ɗin sun je sun gaishesa…
Washe gari aka kawo lefen Maryam daga gidan su Ahamd. Lefe ne na nunama tsara dan an nuna dukiya kam babu ƙarya. Ƙwaƙwalwar Umman neman zautuwa takeyi. Dan kasa jurewa tai yau ma sai kulle kanta tai a ɗaki. Ga dangin Ammah dana Abba nata zuba mata habaici batare da sun duba cewa ƴar uwarsu bace ba. Anyi komai cike da girmama juna da mutuntawa dan suma sun bada tukuyci mai tsoka. Bayan wucewar ƴan kawo lefe Smart ya ɗauki Lulu da AA da Asma’u suka nufi gidan su Lulun. Daddy da su Amrah sunyi farin cikin ganinta, duk da kuwa jiya harda su a ƴan tarbarsu. Basu koma gida ba sai dare. Mommy ma taji daɗin ganinsu. Tana ta tsokanar AA. Hira sosai Smart suka sha da Daddy, dan anan suka yini sai bayan sallar azhar suka nufi gidan Uncle Yousuf. Anan ɗin ma dai hirar aka sha, samun su twins da sukai can yasa Smart da Lulu fahimtar akwai wani abu tsakanin Hussain da Asma’u. Hakan yama Lulu daɗi sosai ita da Smart. Basu bar nan ba sai bayan la’asar. Sun nufi gidan Baba garko inda suka ƙarasa yinin. Itama dai Dada harda kukanta dan ta fahimci dai waɗan nan ma’aurata kainuwa ne dashen ALLAH. Sannan FURAR DANƘO ne damasu ace za’asha farau-farau abune mai wahalar gaske. Jiki luɓus suka koma gida dan Lulu tayi laushi. Ammah taita ma Smart faɗan miyasa bai barta acan ba yaketa yawo da ita haka. Shi dai murmushi kawai yayi yana kallon Lulu dake masa gwalo ƙasa-ƙasa. Washe gari yana tare da Ahmad da Coach, acan ya yini sukasha hirarsu da ubangidansa. Bai dawo gidan ba sai dare dan har Malam na Yakasai yaje ya gaidar bai manta alkairi ba nan ma….
Al’amarin biki ya kankama sosai, Smart ya haɗama amarya gidan mijinta da kaya na kece raini da nunawa tsara. Yayinda aka fara events da aka shirya wanda ya kafa ya tsare ya hana Lulu zuwa ko ɗaya saboda yanayinta. Daga ƙarshe ma da yaga hayaniyar gidan na mata yawa sai ya dinga janyeta zuwa masaukinsa. Acan suke kwana sai da safe ya dawo da ita nan ta yini cikin danginsa. Lulu ta amsa suna matar babban Yaya. Dan komi aka buƙata bata jin ko ɗar zata fidda a jakarta ta bada batare da tabi takan mijinta ba. Sai wasu a ƴan uwa suka fara tsogumin ai ta kankane komai sai abinda taso take badawa. Tun anayin ƙus-ƙus har zancen ya fito fili yakai kunnen su Ammah. A take Ammah ta nuna ɓacin ranta akan hakan, yayinda Smart da shima ransa ya ɓaci ya basu amsa da ai kai da kaya duk mallakar wuyane. Shi kansa a ƙarƙashin say ɗin Lulun yake bama dukiyarsa ba. Ballema ko sisi bai bata ba duk abinda suka nema ta basun kuɗinta ne. Wannan zantukan nasa yasa jikunansu yin sanyi, dama dai cikin dangin Abba ne da ƴaƴan Mama da wasu ana Ummah masu gulmar. Sai aka koma ƴar sinne kawunan jin kunya.
Ana gobe ɗaurin aure akai dinner. Ita kaɗai Smart ya bari Lulu ta halarta. Shima kuma yaje. Dan tare sukaje tana gefensa riƙe da hannunta AA daya maƙale masa da ga hannun su Abdull ɗauke a kafaɗarsa. Sun isa a lokacin da kusan kowa ya gama zuwa. Dan har biki ya fara. Dan haka gaba ɗaya attention na mutane ya dawo kansu musamman yanda mc ke kwarzanta wanene Smart ɗin da matsayinsa a wajen ango Ahmad da ma Amarya Maryam. Nan fa dangin Ahmad ɗin masu ɗan jijji da kai irin na dangin miji suka shiga hankalinsu. Dan sun fahimci abinda sukeji basu yarda ba ashe gaskiya ne. Dan kamanin Smart da Maryam a bayyane suke. Nan fa ƴammata suka ruɗe da ganin matashin ɗan ƙwallon da duniya ke yayi mai ji da kuɗi. Sai dai Lulu dake fama da cikinta tana nane da abunta. Duk yarinyar data kama tana kallar mata miji kuwa zatasha harara. Shiko Smart nata ƙunshe dariya dan yana sane da matar tasa. Amarya da ango sunsha ƙyau har sun gaji, yayinda bakin Ahmad yaƙi rufuwa. Liƙi sosai daya ruɗa hall ɗin Lulu da Smart suka dinga zuba musu harda AA da Ahmad ya ɗaga sama yana sumbatarsa da faɗama mc cewar a sanar kowa ya sani wannan surukinsa ne. In sha ALLAH yanda suka taru anan bikin aurensu haka wataran zasu taru bikin auren AA da matar da zasu haifa masa. Wannan zance na Ahmad yasa kowa dariya a wajen tare da addu’ar ALLAH ya tabbatar da hakan. Ba’a tashi ba Smart ya ɗauki matarsa suka gudu dan taje ta huta saboda bata jimirin hayaniya yanzu….
Washe gari aka ɗaura auren Ahmad Rabi’u Ƙoƙi, da amaryarsa Maryam Mika’il Mawashi akan sadaki naira dubu ɗari biyat bayan sakkowa da ga massalacin juma’a. Ɗauri aure ne daya samu halartar manyan mutane a dalilin gidajen biyu. Tare da ɗunbin masoyan Smart da ga jihohi daban-daban. Anyi walima da yamma. Zuwa bayan isha’i aka shirya kai amarya ɗakinta. Yayinda kaf yayunta harda su Sadiq ƙanana suka taru a falon Abba domin mata nasiha. Tasha kuka sosai har muryarta na dishewa. Dan yayun nata sun mata nasiha mai ratsa zuciya. Bayan an kammala Smart da Salim da Zubair da Kamal suka sakata a danƙarereiyar motar da Smart ya siya mata suka kaita gidan mijinta da rakkiyar mata iyaye guda biyar kawai. Da zasu taho ne ta rungume Smart tana kuka da jera masa godiya. Murmushi yayi a hankali yana mai lumshe idanunsa kafin ya ɗagota a jikinsa. Fuskarta ya riƙe cikin hannayesa yana girgiza mata kai alamar tayi shiru. Daga haka ya shiga gaya mata daɗaɗan kalaman da saida ta saki murmushi. Sannan ya kamo hannun Ahmad ya saka masa nata a ciki ya ɗan bubbuga kafaɗarsa ya fice yana maida hawayen da suka cika masa ido shima. Smart na matuƙar so da ƙaunar ƴan uwansa matuƙa a rayuwa. Akwai shaƙuwa sosai a tsakaninsu duk da bawani sakewa yake da su ba. Dama sauran duk sun fita harma sun shiga mota. Yana zuwa shima ya shiga kawai suka wuce……..✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣3️⃣
…….Washe garin da aka miƙa Maryam gidan miji Mawashi family suka tashi da tashin hankali biyu. Na farko shine gano Huwaila ɗauke da cikin shege na watanni biyar. Tashin hankalin bayyanar wannan ciki kuma yasa Ummah yanke jiki ta faɗi. Inda faɗuwar tata ta zama sanadin samun paralysis. Smart na masaukinsa yana barcin gajiya Lulu a jikinsa ya samu kira da ga Salim. Dole ya shirya ya nufo gidan da Lulu data dage bazai barta ita kaɗai ba. Sun sami gida a rikice. Ko Ummah ba’a ɗauka ba zuwa asibiti sai da yazo ya fara faɗa. Bayan ankai Ummah asibiti suka samu tabbacin ta samu shanyewar ɓarin jiki gida suka dawo da ita bisa shawarar doctor bayan anyi treatment ɗinta yanda ya kamata. Ummah dai an tafi, dan babu abinda ke motsi a ɓarinta na dama sai ido da kai. Amma daga wuyanta zuwa yatsanta ma ƙafa komai cak. Sai ɗayan ɓarin haggun kawai. Babu abinda take sai hawaye. Dan bakin ma idan tayi magana ba’aji sosai sai yawu ke fita babu ko ƙyawun gani.
Smart da Salim suka tsare Huwaila. Zata musu wani kwana-kwana tasha maruka a hannun Smart. Salim ya rufeta da duka da ƙyar aka tsaida shi saboda lalurar dake a jikinta. Wahalar da tasha yasata faɗin gaskiyar cewar saurayinta ne ya mata lokacin suna tare da Umma a gidan Kawu Jibirin, idan tace ta tafi makarantar islamiyya sai ya ɗauketa a hanya su tafi hotol ko ɗakin abokansa. Ran kowa ya ɓaci Abba harda hawaye yana jama Umma ALLAH ya isa da jin nadama bisa nadama akan aurenta. Dan bai tsira da komai ba sai baƙin ciki da tashin hankali tun daga ƙuruciya har zuwa yau. Garama yanzu da Smart ke ƙoƙarin dawo da su Salim a hayyacinsu. Dan a yanzu haka jira yake a kammala bikin nan ya gyarama Salim shagunansa da suka ƙone. Smart yasa an nemo wanda yayma Huwaila ciki tare da iyayensa. Da farko ya musa harda cewa shi baima taɓa ganin Huwaila ba, sai da Smart yay masa jan ido harda maruka biyu a gaban iyayensa babu ko kunyar idonsu sannan ya faɗi gaskiya, amma yace ai bashi kaɗai bane tana kaima wasu. Huwaila ta sanya kuka da rantsuwa da shi kaɗai take tarayya, hasalima shine ya fara saninta ɗiya mace, tana ma da shedar hakan. Ansha rikici sosai har sai da Huwaila ta kawo recording na wayar da suka dingayi da ta dinga ajiyewa sannan fa shegen yay laushi. Inda aka tsaida magana da zaran ta haihuwa za’a ɗaura musu aure. Sauran ƴamatan gidan kuma ya basu tabbacin nan da wata uku kowacce ta kawo mijin aure in ba hakaba shi zai zaɓo musu. Hakan ya saka iyayen jin kwanciyar hankali. Dan sai ga Mama sarkin ruɗiya yau na sakama Smart albarka. Saboda ba ƙaramin tayar mata da hankali batun cikin nan na Huwaila yay ba, dan itama tana da ɗaya a ɗakinta mai rawar kan tsiyar da giggiwa. Haka ta tasa ƴaƴanta gaba wanda basuyi aure ba tana roƙonsu ALLAH Annabi su taimaka mata su rike mutuncin kansu karsu kasheta tun lokacinta baiyi ba kamar yanda Huwaila ta zama sanadin Ummanta. Sun daiga yanda tarbiyyar ƴaƴan Ammah a gidan ta jawo musu alkairi…..
Samun lafawar ƙurar biki ta bama Smart nutsuwar fuskantar ƴan uwansa. Yayinda ya nutsu wajen nemawa ƴan uwansa maza da matan ma abinyi. Tare da zagaye dangin mahaifiyarsa dana mahaifinsa kaf yay musu alkairai masu tsoka da yaketa samun albarka shida zuri’arsa. Shine har dangin Mama dana Aunty Amarya, dan ita Umma danginta sune dangin Abba sai dai na ɓangaren mahaifiyarta. Gefe ɗaya kuma ya samu damar gina wasu manya-manyan mall guda biyu da kafa business daban-daban. Tare da yin amfani da ƙungiyar Lulu ya tallafama yara da ɗan yawa akan karatu. Masu shaye-shaye a ciki ya kaisu rihab. Dan Nadiya dake ta lallaɓa rayuwarta a yanzu tare da Ummita tsaye suke akan ƙungiyar. A cikin wannan halin bikin Ummita da Usman ya tashi suma. Haka Lulu taita ƙoƙari nan ma akayi komai da ita. Ta kuma bama Nadiya shawara akan ya kamata itama ta samu miji mai irin ciwonta suyi aure tunda yaron data haifa ya rasu. Ranar Nadiya tayi kuka sosai, tare jerama Lulu da Smart har ma da su Uncle Yousuf addu’oi. Dan yanzu ta koma gidansu a dalilin sanya baki da baba Garko yayi a zancen, babu kuma wanda take ganin mutunci da kima yanzu a duniya sama da Lulu da Smart. Amaryar Baba Garko ma ta shigo cikin tawagar masu kula da ƙungiya. Hakama Tajuddeen da a yanzu ya sakama kansa haƙuri game da al’amarin Lulu yana bada gudunmawa. Shima dai an saka bikinsa da ƙanwar amaryar mahaifinsa. Tunda ya lura yarinyar na masifar sonshi mahaifiyarsa da su Baba Garko suka bashi shawarar ya aureta kawai ya rufama kansa asiri, dan yanzu ba gida duka bane zai nema aure a bashi saboda tabon da mahaifinsu ya bar musu a cikin al’umma. Kowa ya zata Dada zataƙi. Sai gashi babu ko ja’in ja ta amince harda bada gudunmawar ta…
_______★
Hutun Smart ya ƙare zasu koma England sai dai Ammah tace bada Lulu ba. Dan a gida zata haihu wannan karon itama taga gatan da kowace ɗiya ke samu. Ba haka yaso ba dan haka ya dinga fushi. Ammah ko ta tattarashi ta watsar da faɗin yama fashe mana. Mawaddat ce dai babu inda zataje sai ta haihu tunda watan gobe ne haihuwar. Har kawo zancen AA zai shiga makaranta yayi amma Ammah tayi mirsisi da shi. Sai ma tace masa ya tafi da AA ɗin su zauna Lulu ce dai babu inda zataje. Babu yanda ya iya haka ya tattara rai a jagule ya tafi Lulu na faman masa dariya da gwalo. Dan ita farin ciki take da barinta a wajen Ammahn ta. Tana so da ƙaunar baiwar ALLAHr nan a rayuwar. Itama kuma Ammahn na nuna mata ƙauna mai tsayawa a rai. Idan ka gansu tamkar ba surukai ba. Wannan soyayyar tasu daga ALLAH ce kawai za’ace..
Bayan wucewar Smart babu jimawa aka ƙarasa masa ginin katafaren gidansa da mutane keta magana akansa duk da basu san kona wanene ba. Dan hatta Lulu bata sani ba. Ammah da Abbah da Ahmad da Coach sai Uncle Yousuf ne kawai suka san gidan na Smart ne. Kamar abinda Lulu ke jira kenan ta fara naƙuda. Hankalin su Ammah ya tashi dan cikin dare al’amarin ya tasar mata. Gashi Ammah ta fahimci Lulu nada masifar tsoro ga kuma ta da Naƙuda mai wahala. Dole suka wuce asibiti a daren nan bakunansu da addu’a. A wannan karon ma dai cs aka shirya yima Lulu. Tunda Asma’u ta kira Smart ta sanar masa hankalinsa ke’a tashe. Tun a daren nan ya fara neman mafita dan ya tabbatar bazai taɓa iya haƙuri ba sai yazo Nigeria. Da ƙyar ya samu aka masa alfarmar kwana goma. Aiko babu ɓata lokaci ya shiga shiri…
Alhamdullah an samu nasarar cirema Lulu yara biyu mata masu kama da mahaifinsu tamkar AA. Zokaga farin ciki da murna a wajen familyn nan guda biyu da suka zama tsintsiya maɗauri ɗaya a yanzu. Sai dai murnar tasu ta taƙaita ne kasancewar Lulu na cikin wani yanayi mai ban tashin hankali. Dan har Smart ya iso bata dawo hayyacinta ba. Hakan ya tada hankalin kowa da bada mamakin kasancewar a yanzu ansan cs ana yinsa ne ma idon mutum biyu. Koda Smart ya iso shi bata yaran yake ba, ta matarsa yake yi. Dan baiji nauyin kowa ba ya durƙushe a gaban gadon da take kwance samɓal kamar wadda ta mutu ya saki wani irin kuka mai ban tausayi. Yanda ya kife fuskarsa akan tafin hannunta yana kuka hawayensa suka jiƙe mata hannu. Haƙuri likitocin keta bashi dace masa addu’a take buƙata. In sha ALLAH kuma zata iya farkawa a kowanne lokaci numfashinta ne kawai yay nisa. Ba Smart kawai ba hatta Daddy hankalinsa a tashe yake. Dan yana tuna a dalilin haihuwarta ya rasa mahaifiyarta itama. Baba Garko da Abba ne suketa lallashinsu da basu baki. Har dare babu wani bayani akan Lulu. Ga Smart ya kafa ya tsare ko nan da can baya gusawa, salla kawai ke tada shi a ɗakin. Cikin amincin ALLAH gabannin asubahi Lulu ta farfaɗo. Rikicewa Smart yayi dan farin ciki. Ya rungumeta jikinsa na rawa ga hawaye..
Cikin ɗaga idanunta da kyar da shafo fuskarsa murya ƙasa-ƙasa ta furta. “Mr A!”.
Rikicewa yay da farin ciki yana tattaɓata da rungume hannunta a ƙirjinsa hawaye fal idanunsa ya amsa da “Na’am Mawaddatan’warahmah!”. Wani irin murmushi mai tsayawa a rai ta sakar masa tare da maida idanunta a hankali ta sake lumshewa, hannunta ya saki a hankali. Wani irin ƙara Smart ya saki yana mai girgizata da sambatun faɗin, “Dan ALLAH kar kimin haka Mawaddat, karki tafi ki barni, kece rayuwar Aliyu kece farin cikinsa. Ni nake fata na rigaki mutuwa bake ki rigani ba. Ki tashi dan ALLAH na roƙeki”.
Kukansa da sambatunsa yay matuƙar tada hankalin kowa a wajen. Dan Daddy ma luuu ya tafi zai faɗi sai da aka taroshi. Da ƙyar aka fiddo Smart a ɗakin likitoci suka rufu akan Lulu……..✍️
🙉🙉🙉Munga Boni
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣4️⃣
____________
………Awannin da suka gabata sun tafine da sautin bugawar zukatan waɗan nan ahali. Kafin kowa ya samu nutsuwa a dalilin farfaɗowar Lulu. Ba’a bari an shiga inda take ba sai Smart kawai. Dan shikam a ranar ma tare suka kwana. Ko yaya ta motsa ya dinga tambayarta minene damuwarta kenan har saita sakar masa murmushi. Sai washe gari ƴan uwa da abokan arziki suka samu ganinta. Daddy ji yake kamar ya haɗiyeta dan farin ciki. Duk wani masoyinsu da uban gayyar sai yau suka samu nutsuwar kallon baby’s. Yayinda aka koma kuma taya juna murnar samun ƙaruwa.
Salim shi Smart yasa yayma yara huɗuba a kasancewarsa babba. Itama Lulu sai a ranar ta samu ganin abinda ta haifa. Cikin ƙarfin hali da magana ƙasa-ƙasa take faɗin, “Mr A wannan karon ma kamin wayo, su duka kai suka biyo”.
Murmushi ya sakar mata yana wani ɗage gira sama da amsa mata da cewar, “Hakan na nufin na fiki jarumta a filin yaƙin ƙasa da ƙasa kenan. Next time ma ƴan uku zakiyi in sha ALLAH”.
Da sauri ta kauda kanta gefe tana faɗin, “Ai kai dama ba’a hirar arziƙi da kai. Mutum ko gama dawowa hayyacinsa baiyi ba kake wani kira masa haihuwar ƴan uku”.
Dariya ya sanya mata Nadiya na tayashi. Dan duk tana ɗakin suke wannan taɓarar… Dada da ciwo ya sake fidda tsufarta ta taƙarƙara da ƙyar tazo asibitin da duba Lulu. Lokacin da taga ƴan tagwayen nan sai da hawaye suka cika mata ido. Dole abubuwa su rincaɓe musu dan rabon yaran nan kaɗai ya isa ya zama sanadin kaudasu a duniya. Gashi nan cikin shekara biyu da rabi a auren nasu Lulu nada yara uku…
Alhmdllh Lulu ta samu kanta sosai kasancewar jikinta mai ƙyau ne baya riƙe ciwo. Kwananta shida aka sallamesu suka koma gida. Dan ta matsa akan ita a sallameta ta gaji da zaman asibitin nan bata son warin. Haka aka sallamota suka nufi gida. Sai dai maimakon gidan Abba sai taga an wuce da ita katafaren gidan da mijinta ya gina batare data sani ba. Duk da sun taɓa wucewa ta gaban gidan kasancewar a anguwarsu ta hotoro GRA ne har taita santinsa. Ashe wai nasu ne. Koda ta jiyo tana kallon Smart sai ya kama kunnesa yana wani ɓata fuska kamar AA na fushi. Murmushi kawai tayi tana mai sinne kanta dan suna a tsakkiyar mutane ne.
Gida bai sake rikita kowa ba sai da suka shiga cikinsa. Abun ba’a cewa komai kawai. Lulu na son keɓewa da mijinta sai dai babu dama. Dan gidan cike yake kasancewar su Ammah sunce fa sai anyi taron suna. Washe gari aka raɗama ƴan biyu suna. Inda sukaci sunan *_Ayshatul-humairah da Hafsatul-Ikram_*. Ƴan biyu Aysha da Hafsat sunyi goshi matuƙa. Dan kwai da kwarkwata na dangin Lulu da Smart musamman ƴan FURAR DANƘO C-BOX. AREWABOOKS, ZAFAFA FANS dama ƴan bayan katanga masu karatun bati sun zo a gayyar SOƊI🤣🥱 (A daure azo a biya 400 ne, duk 1k babu yawa bama son halin dangin Sulaiman Tsule ƴan bati. Dan nidai babu ruwana biyana za’ai🤪😜). An raƙashe an ƙwalle a wannan taron suna yayinda amaryar jego da jariranta sukasha ƙyau har suka gaji. Shi kansa angon jegon badaga baya ba kam. Munci hinkafa iya hinkafa. Munha zoɓorodo harda kajin gidan gona masu tsokar gaske. Ga halawa da biskin duk an bimu da su a ledoji. Kai al’amarin dai ba’a cewa komai dan an nuna halin girma. Sai muce ALLAH ya raya Ayshatu da Hafsatuwa….
Har washe gari gidan nan cike yake da mutane. To su Xoxo anga hinkafar banza anƙi tafiya🥱. Huguma da Rano da Mamu kam harda rantsuwar su sai Lulu tai arba’in zasu wuce, yo anga gida ginin gilashi🤣. Nace kunji abin kunya Zafafa dai sai an nuna hali a ko’ina😏🚶, alhalin hinkafar nan fa dai kowa nada a gidansa, gilashi kuwa kowa akwai a windown gidansa. Amma dai bari mu bincika o’e da o’e kodai-kodai 🥱. (I love you Zafafa’s😘😘😘❤️💞🙏).
Shatara ta arziƙi kam dai Lulu ta sameshi a wannan haihuwar. Dan Nadiya da Ummita da amaryar Baba Garko da Maryam amarya sune tsaye akan duk wani gift data samu. Tun a wajen hotuna bata sake saka mijinta a ido ba sai a daren na washe gari ya fidda kunya dai ya shigo har ɗakinta. Su Ummita dake baje suna buɗe gifts suka suka fara rige-rigen fita. Idanu Lulu dake da ga kwance AA na gefenta zaune yana fitinar a bashi Baby ta ɗago a hankali ta sauke a kansa. Shima ita yake kallo da yaransa guda uku dake gabanta reras. Lallausan murmushi ya sakar mata yana mai lumshe ƙyawawan idanun nan nasa da take kira na maciji tare da ɗaga kafafunsa a sannu-sannu ya cigaba da nufota cikin takun ƙasaita da kasala tamkar mai irga steps ɗin nashi. Dai-dai yana isowa ta yunƙura zata tashi zaune ya girgiza mata kansa yana mai kaiwa zaune a bakin gadon da kama kafaɗunta ya maidata ya kwantar yana kaɗa mata kansa. Bata da zaɓin daya wuce komawar ta kwanta. Baice da ita komai ba sai hankalinsa da ya maida kan AA. Cike da kulawa ya ce, “Waya saka Baban Ammah kuka ne?”.
Cikin shagwaɓa AA ya nuna Lulu, dan har yanzu shi maganar tasa sai a hankali ce. Dan ma ɗan zamansu a Nigeria ɗin nan ya fara samun bakinsa kasancewar gidan Abba gidan yarane. Balle shi da ko yaushe yana hannun yaran gidan kowa ji yake da shi saboda ƙyautatawar iyayensa. Kaɗan Smart ya ɗan waro idanu waje da faɗin, “Kai-kai Maah-maah ce”. Kai AA ya ɗaga masa yana wani sake ƙwaɓe fuska.. “Ayya Kakan Papa yi shirunka ƙyale Maah-maah kaji ko. Bazamu saya mata kayan daɗinmu ba ai ko?”. Nan ma AA ya ɗaga kansa dan yana jin magana sarai abinsa. Gyara masa zama Smart yayi tare da ɗaukar Hafsat dake a kusa da shi ya ɗauramasa a saman cinya, sai dai bai sakar masa ba tana a hamnunsa. A take yaron ya hau dariya yana nuna Aysha wai itama a ɗaura masa. Haka Smart ya biye masa itama ya ɗaura masan. Ita dai Lulu na kallonsu kawai, dan a yanzu tana sake fahimtar irin so da ƙaunar da mijin nata kema yara ta dabance. Sai da yaran suka ɗan jima a cinyar yaron sannan ya saukesu ya kwantar da su yace ya kwanta kusa da su ya musu wasa.
“Ni dai kada ya tsokale min idanun yara gaskiya. Har yanzu ban gama dawowa a hayyacina ba fa”. Lulu ta faɗa cikin shagwaɓa harda wani ɗan tura baki. Dariya ta bashi ma shi, dan haka ya juyo yana kallonta gira a ɗage ya ce, “Oh really?!”.
“Kai ne shaida ai, tunda kai kafi kowa shan kuka”.
Kansa ya kauda gefe yana murmushi da faɗin, “Oh ni Aliyu. Na shiga tara kuma da gorin yarinyar nan. Ke da baƙya raye a lokacin ya akai kika san haka?”.
Murmushi ta saki mai bayyana haƙwara. Ta ce, “Likimo nayi fa duk ina jinka. Dan na sake tabbatar da wanene mijina. Ashe ragone shi a kan lamurana”.
Yanzu kam dole dariyarsa ta fita da sauti. Ya zuba mata mayun idanun nan nasa yana sakar mata wani murmushi mai sanyi da fasa zuciya. A can ƙasan maƙoshi yana mai dimtse hannunta cikin nashi da ƙyau ya ce, “Kin san kuwa matsayin da Mawaddat Jiƙamshi ke da a zuciyar Aliyu! Wannan sirrin ALLAH ne kawai yasanshi Baby luv. Kin fa gama mamaye ko’ina da ina baki ragema wata koda ƙanƙanin fili ba. Har tsoro nake ji kada wataran ƙaunarki ta fasa zuciyar ɗan bawan ALLAHn nan ma”.
Tuni ƙwalla sun cika mata idanu, zaune ta tashi tana mai juya kwanciyarta zuwa jikinsa. A tare suka saki ajiyar zuciya da lumshe idanunsu suka buɗe duk a lokaci ɗaya. Akan yaranta ta fara sauke nata kafin ta juyo gareshi hawayen da suka taru mata na sakkowa a hankali bisa ƙyaƙyƙyawar fuskar ta. Da sauri ya wara idanunsa zaiyi magana sai ta sakar masa murmushi da girgiza masa kan alamar kada yace komai.
“Aliyu!”.
“Uhyim Mawaddatan’warahmah!”.
“Kai ɗan aljanna ne da izinin ALLAH”.
“Tare ai zamu shige in sha ALLAHU”.
“Da’ace wani ɗan adam nada damar buɗema ɗan uwansa nan dana buɗe tawa ka ga matsayin ka a ciki” tai maganar tana ɗaura hannunsa a saitin zuciyarta. Idanunsa da sukai rauni sosai ya lumshe da sake buɗewa a kanta. “Kin mallaki Aliyu Hydar da komansa Mawaddatan’warahmah. Na jima da sanin kema kin mallaka masa zuciyarki. Sai dai ban san miyyasa kika zaɓi ɓoyewa ba baby luv. Salonki na azabtar dani matuƙa”. Dariya ta ƙyalƙyale masa da ita tana ƙoƙarin tashi ya hanata. Sai ma sake matseta da yay cikin jikin nasa har sai da tai ƴar ƙara da faɗin, “Wash ciwona”. Da sauri ya saketa a rikice, ta ko kwashe masa da dariya tana masa gwalo. Sai ya ƙwaɓe fuska cike da shagwaɓa ya ce “Zan rama ne ai”.
“Sai dai wani karon wannan kam nayi winning”.
“Ba komai, ai da kai da kaya duk mallakar wiyane.” yay maganar yana mai lakace mata hanci. Ita kuma taja kumatunsa da faɗin, “Yaushe Aliyu ya fara ɓoyewa Mawaddat sirrikansa?” ta ƙare faɗa tana kallon ɗakin. Ya fahimci mi take nufi. Dan haka ya saki ɗan murmushi da kallon ɗakin shima. “Aliyu bai taɓa ɓoyema Mawaddat sirrinsa ba. Ya mata hakanne kawai domin supricing ɗinta, kuma Alhmdllh burinsa ya cika, wannan shine gidan Mawaddatan’warahmah da Aliyu da zuri’ar da zasu tara in sha ALLAH.”
Hawayene masu ɗumi suka gangaro a idanun Lulu dake kallonsa ko ƙyafta idanu batayi. Kallonta yay da sauri. Zai yi magana ta ɗaura yatsarta akan lips ɗinsa ta ce, “Shiii!!. Lokacin Mawaddat ne”.
Yanda tai maganar cikin raɗa sosai ya sashi sakin murmushi…..✍️
😁😁😁😁To nima bari na ɗan murmusa
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣5️⃣
________
*_INNALILLAHI WA’INNA ILAIHIRAJI’UN 😭😭😭_*
_ALLAH yayima *MARUBUCIYA FAREEDA ADO GACHI* rasuwa. Ya rabbi ka gafarta mata ka yafe mata kura-kuranta. Ayyukanta na alkairi su zama fansata domin rahamarka ya *UBANGIJI. MARUBUCIYA* ce data taka rawar gani a harkar rubutu da alƙalami da duniyar rubutu bazasu manta da ita ba. Tana cikin tawagar manyan marubutan nan na *MACE MUTU* a littafinsu mai suna *HANNU DA YAWA…..* da wasu ire-iren su. Ta rubuta littatafai ita kaɗai kamar haka._
*MEKE NAN?*
*RAYUWAR MATA*
*ƳAN UBA*
*NI KO SHI*
*RA’AYINA NE*
*TUBALIN TOKA*
*_ALLAH kai mata RAHMA damu baki ɗaya. 🙏🙏_*
*_MADUBINA A HARKAR RUBUTU TA TAFI 😭😭😭🙏_*
_____________
…….A bazata ya ji saukar lips ɗinta akan nasa. Daburcewa ya nema yi kasancewar anfa jima ba’a haɗu ba. Dama ɗan Ammah a wuya yake. Sai da ta gama rikita masa lissafi da salon da bai taɓa sanin ta iya ba sannan ta nema janye jikinta. Shi kuma a sannan yace bai san zancen ba. Dan ta riga ta ɓallo MAZAN FAMA. Murya a sarƙe yana ruƙota ya furta “Please Mawaddatan’warahmah”.
Murmushin mugunta ta sakin masa tana kai bakinta a saitin kunnesa ta furta, “Jego muke fa”.
“Bayan kin gama jigata ni”.
“Yada karaya haka MAZAN FAMA”.
“Ki ɗauka kawai na zama rago ko MATAN FAMA”.
Dariya Lulu ta kwashe da shi. Kamar zai saki kuka ya ce, “Ki kasheni ki huta kawai”.
“Idan na kashe Aliyu dawa za’a ganni a filin yaƙin ƙasa da ƙasar kuma ni Mawaddat”.
Harara ya ɗan sakar mata yana kaiwa kwance dan gaba ɗaya jikinsa babu wani ƙarfi. Yaransa ya zubama ido kawai dan AA ma yayi barci a kusa da twins.. Mintsini ta kai masa, yay shiru, ta sake ya sake mata shiru, ta sake kai hannu a karo na uku ya damƙe hannun tare da birkiceta. Rikitata ya shiga yi tare birkita mata lissafi da zazzafan salonsa. Sai ga Lulu na roƙonsa harda kukanta akan ya rufa mata asiri yau fa kwananta tara da haihuwa. toshe kunnuwansa yay kamar baya jinta, sai da ya tabbatar ta tsorata matuƙa sannan ya harareta yana komawa gefe. Sai kuma ya koma yimata dariya ganin yanda ta gama fita a hayyacinta da tsoro. ƙaramar ƙwafa yay da faɗin “Gobe ma ki sake takalata zaki sha mamaki dan sai kinga ƙarshen tsokala.”
Baki ta tura masa tana harararsa, da sauri ya kai mata cafka, ta dire da gudu daga gadon. Dariya ya kwashe da ita harda hawaye itako tana harararsa baki a sama…..
Duk shagalin da aka sha sai da aka kaima Umma labari, hawaye kawai take zirararwa. Ga shi dai Aliyu yakai inda ta jima tana yaƙin, yayinda ita take kwance sai an kwantar an tayar. Miji ya saketa ƴaƴan nata ma sai wanda ya ga ALLAH yake tausaya mata. Gashi su dukansu sun koma ƙarƙashin alfarmar maƙiyin nata. Kallon Ammah kawai na ɗaga mata hankali. Dan daka ganta kasan Alhmdllh komai ya zauna dole a kirata uwar sarkin gida. Suna da matsayin data jima farautar samu. Huwaila harda nuna mata video ɗin gidan Smart. Nan ma saita ɓarke da kuka. Babu kunya Huwaila ta sanya dariya tana faɗin, “Su Umma dai ana kwancen ma baza’ai dana baƙin ciki da cigaban wasu ba”. Tana gama faɗa ta miƙe da cikinta tirƙai-tirƙai da ke saka jinin Umma sake hawa a duk sanda ta kalli Huwailar tayi wucewarta yayarta na mata faɗa bata ko saurareta ba…..
★★★
Duk yanda Smart yake kwaɗayin zama kusa da iyalinsa dole ya shirya ya koma saboda cikar kwanakin da aka bashi. Ya tafi ya barsu da kewa kamar yanda shima ya tafi da kewarsu. Haka Iya Tabawa ta cigaba da kula da Lulu. Yayinda Asma’u ta dawo nan dan gidan yay masu girma duk da an zuba ma’aikata kamar su maigadi mai gyaran filawoyi mai wanki harma da driver da mai share-share da sauransu. Sannan Huwaila ma kusan tana anan ne ita da Nadiya. Hakan ya ɗan ragema Lulu raɗaɗin rashin mijinta a kusa da ita. Sai dai akoda yaushe suna maƙale a waya ana video call. Ammah na leƙosu akai-akai, hakama aunty Saliha. A haka sukai arba’in zuwa lokacin ta gama gyagijewa. Ga gyaran Iya Tabawa tana samu mai lafiya dan ita kanta tana jinta on top. Ta zagaye dangi itace har Abuja, kafin ta fara shirin komawa dan Smart ya ishi kowa da damuwarsa. Ammah dai data gaji da yawan ƙorafinsa ta ce ta shirya ta tafi wajen mijinta kozai barsu su huta. Kunya abin ya bama Lulu ma ita. Shiko ta fahimci ko’a ƙwallar rigarsa. Tare da Asma’u suka wuce da Iya Tabawa. Mai gayya da aiki ne da kansa yaje tarbarsu airport, da mamaki yake kallon Asma’u dan bai san da ita za’azo ba. Lulu bata taɓa sanar masa ba har taima Asma’u komai-da-komai na tafiyar. Bai iya cewa komai ba ya kwashesu suka wuce yana ɗauke da yaran duka, sai da Asma’u ta amsar masa AA dan taga sun masa yawa. Tsaff suka samu gidan nasu harda abinci ya tanadar musu. Dan haka babu ɓata lokaci sukayi wanka suka baje. Asma’u ce ma dai keta faman ƙauyanci da santin gidan suko suna mata dariya. Shi dai Smart na manne da yaransa kamar wani yace zai ƙwace masa su, dan gaba ɗaya hankalinsa na kansu ne.. Sai narkakken kallon da yake bin matarsa da shi lokaci-lokaci a kaikaice wanda ita kaɗai ta fahimci abinta. Dan haka taɗan shiga tsoro dan tasan yau kam saita ALLAH wai biri a hannun bamaguje. Gashi tasha gyara kala da iri da ita kanta tasan sai tayi bayani da yaran Jiƙamshi yau kam.
Kamar yanda tai hasashen kam ta ɗanɗana kuɗarta, yayinda Smarty ya rikice mata tare da sanya mata albarka babu adadi. Tattali kam ta shashi a wannan yinin, gashi dama babu inda ya fita dan haka suka yini a ɗaki da ƙyar yake barinta ta leƙa su Iya Tabawa kodan Asma’u dake fama da baƙunta. Yayinda ya barta da jin kunyar Iya Tabawa, shiko ko’a ƙwallar rigarsa. Bayan dawowarsu da sati uku ya fara nemawa Asma’u gurbin shiga jami’a ta fara, sai dai kullum tana manne da waya suna shan soyayyar su da Hussain ɗin ta, idan kuma ya bushi iska yakan shiryo yazo UK ɗin ya mata kwana biyu. Tayi farin ciki da hakan sosai dan ita mai son karatu ce dama. Shima AA an sakashi makaranta, sai dai ba boko bace ta addini ce da wani balarabe maƙwafcinsu ya ɗan buɗe domin yaran musulmai. Lulu ta cigaba da shayar da yaranta cikin ƙoshin lafiya da kuzari, yayinda suketa ƙara wayo da ƙyawu masha ALLAH. Kamaninsu da mahaifinsu da AA nata ƙara fitowa….
_________★
Sosai bashi da lafiya. Ya wani irin fita a hayyacinsa tare da yamushewa kamar wani tsoho dan ko Baba Garko bazai nuna masa tsufa ba a yanzu al’amarin zammamaki. Duk wanda yasan Sulaiman ya ganshi a yanzu zai iya dire rantsuwa da bada tabbacin bashi bane. Ya bushe a tsaye ƙwarai da gaske. Tunda aka gama shari’arsu aka kaisa wani mugun jail sau ɗaya Hajiya Turai taje dubashi, ba komai ya kaita ba ma sai amsar takardar sakinta. Dan amaryarsa ita ta samu nasarar amsa tun randa aka yanke musu hukunci. Da ƴaƴansa duka taje, duk da da ƙyar ta samu Tajuddeen ya bita. Ganinsu ba ƙaramin tayar masa da hankali yayi ba ya dinga kuka har suka taho. Sai Daddy dake dubashi duk bayan watanni biyu, amma ƴan uwansa da Baba Garko tun randa aka kamashi basu sake waiwayarsa ba.
Abinda Daddy ya gano a bincikensa saboda hankalinsa ya tashi da ganin yanda Sulaiman ɗin ya takwarkwashe a cikin watannin da basu gaza goma sha uku ba shine allurar guba akai masa da ke cinyesa a tsaye. Ba kowa bane kuma ya harba masa wannan tsiyar sai abokan huɗɗarsa turawan nan. Dan takanas suka zo Nigeria domin hakan garesa, acewarsa amfaninsa ya ƙare garesu kuma. Wannan allurar ce keta faman cin jikinsa a tsaye batare da kowa ya fahimta ba sai su waɗan da aka haɗa kai da su sukai masan. Tun ciwon na cinsa a tsaye har takaisa ga kwanciya a cikin asibitin jail ɗin. Watansa kusan takwas yana wahalalliyar jiyya kafin ALLAH ya amshi rayuwarsa. Rasuwarsa ta zagaya kowace kafar yaɗa labarai, wasu na masa addu’a wasu na ALLAH wadarai da faɗin sai aje kuma a fuskanci kamun ALLAH. Tsakaninsa da Rasuwar Dada wata biyu ne, dan tunda aka sanar musu sanadin mutuwar Sulaiman bata sake lafiya ba, da ga ƙarshe dai itama sai da ta bisa. Garko family sunji wannan rashi matuƙa. Dan Baba Garko yasha kuka shima har sai da ya kwanta asibiti. Lulu ma tazo, sai dai daga ita sai twins tazo. Satinta uku ta tattara ta koma.
(Sai muce ALLAH ya gafartama Dada da iyayenmu baki ɗaya 😭👏).
*_YEARS LATER_*
Barcinsa yake hankali kwance kansa a saman cinyarta. Yayinda ita kuma ta nutsu a masa gyaran kansa. Da farko hira sukeyi a hakan. Sai dai tunda taga barci ya ɗaukesa ta canja akalar gyaran gashin zuwa kitso kasancewar ya tara suma sosai a kan nasa. Sai dai normal askine a kansa ba irin na rashin mutuncin nan da aka san ƴan ƙwallo da shi ba. Tsaff tai masa kitso guda takwas tana kwasar dariya. Hakan bai mata ba ta zame kansa a hankali zuwa saman filo taje gaban mirror ta kwaso kayan kwalliya. A hankali ta zane masa fuska ya fito ras kamar wani mace. Sannan ta fara zuba masa hotuna. Kukan autanta da take jiyowa da ga falo ya sata ajiye wayar ta fita. Ilai kuwa shi ɗinne dan a hanya suka haɗu yana kuka.
“Kai kai waya taɓa min Ubana haka?” ta faɗa tana riƙosa yaron da bazai wuce shekaru uku ba zuwa jikinta. Cike da shagwaɓa ya ce, “Ba aunty Hafcy bace ba. Wai dan nace mata Hassatu shine ta mintsineni da rankwasar min kaina”.
Daƙyar Lulu ke danne dariya, dan kowa a gidan yasan masifar Hafsat ta dabance. Sam bata gado Ammah ba itakam. Gaba ɗaya a hallaya ita ta biyo. Sannan bata yarda a kitata Hafsatu ba. Tace sunan mutanen da ne ita Hafcy gayu take so…….✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆’𝙊…..!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣6️⃣ 🔚
…….Tun haihuwarsu sukaso ɓoye mata suna, Ammah tace a kirata da sunanta bata son wannan ɓoye-ɓoyen. Dole ake kiranta da hakan, itace dai bata iya faɗa sai tace mata Ammah. Smart kuwa shine ya laƙa mata Hafcy gayu saboda ƴar gayence ta gaske. Duk da shekararsu ta shidda kenan itada Hassanarta Aysha iyayi a wajenta ba’a magana kamar wata babba can. Ko shi Smart ɗin yace mata Hassatuwa fushi takeyi kota sanya kuka. Hannunsa taja zuwa falon, inda sauran yaran suke kowa da hidimar gabansa. AA shi dama boss ne (like father like son), komai na ubansa bai bari ba. Baya son hayaniya bayi da yawan magana. Idan kaji bakinsa a gidan nan to al’amari yakai intaha, ga jarabar son ƙwallo da kallonta. Shekararsa takwas kenan da ƴan watanni. Sai ƴan biyu Aysha da Hafcy gayu. Bayan su ta ɗan huta kusan 3years kafin ALLAH ya kawo cikin auta dan tace daga shi fa Alhmdllh ta gama duk da dai Smart yace akwai sauran Ahmad bata gama ba. Shi auta sunan Uncle Yousuf yaci. Shikam akwai fitina, dan halinsa da Hafcy gayu iri ɗaya ne, itama Aysha bajin magana take ba, sai dai nata wani lokacin takan zama irin AA ba ko yaushe ta damu da shiga hayaniyar ba sai idan ita taso.
“Wane ɗan jakar uba ne ya dakar min Babana?”.
Lulu ta faɗa babu alamar wasa a fuskarta. Da sauri Aysha ta nuna Hafcy. “Wlhy itace Maah-maah. Yarinyar nan ta fitini kowa a gidan nan, dan ALLAH a maidata Nigeria wajen Ammah”.
“Eh eh anji ɗin a maida nin, wake tsoron zuwa Najeriya ɗin ƴar iyayi kamar ma an kasa da ke”. Hafcy ce mai maganar cikin zaƙalƙalowa da tsiwa kamar su Lulu ana yarinya. Dan ita kam ko AA bata ragawa balle wata Aysha da suke kai ɗaya. A harzuƙe Ayshan ta miƙe tana huci itama da cewa, “Wai kaina zaki dawo halan. Kin san dai karanmu babu daɗi wlhy fasa miki baki zanyi bar ganin Papa mai goya miki baya yana gida ehe”.
“To gwada idan zaki iya”. Cewar Hafcy.
Tsaki mai ƙarfi AA da ke danna tab.. ɗinsa yana game na ball ya buga. Cikin jin haushi ya dubi Lulu da al’amarin yaran ya girmeta. “Maah-maah dan ALLAH kice ma ƴaƴanki su wuce ɗakinsu ALLAH sun isheni da hayaniya. Yaran nan suna bani ciwon kai ni gaskiya Nigeria zan koma. Gara naje wajen Daddy da Mamy”. (Ahmad da Maryam) dan kuwa ɗan gaban goshinsu ne. Ga kuma alƙawarin ALLAH ya cika sun haifa masa mata mai suna Rasheedah sunan mahaifiyarsa ana kiranta Nu’aimayah.
Cikin ɗoki auta da suke kira Uncle You ya ce, “Yaya nima zanje ka kaini wajen Mammah”. (Asma’u. Dan itama anyi bikinsu da Hussain yanzu haka tanada yaronta da yaci sunan Daddy). Fitowar Smart ya hana Lulu bama AA amsa. Gaba ɗayansu suka juya suna kallonsa saboda gyaran muryar da yayi. Aysha ce ta fara waro idanu waje. Yayinda Hafcy gayu ta dafe baki tana dariya. Duk rashin son hayaniyar AA sai gashi ya kwashe da dariya da faɗin, “Oh oh Papa waya maka kitso da kwalliya?”.
Cikin mamaki Smart ya kai hannu ya shafo kansa da dama yake jin duk ya ɗaure masa. Ilai kuwa sai ga kitso. Da sauri ya kalli sashin da Lulu take tana faman kwasar dariya. Su Aysha na tayata. Babu shiri ai ya nufi mirror dake cikin falon….
“Babbyyyy luvvvvvvv!!!” ya faɗa da ƙarfi ganin aika-aikar da tai masa. Mi yaran zasuyi in ba dariya ba kuwa. Yayinda Lulu ta arta da gudu zuwa bedroom shima ya take mata baya. Suko yara nata dariyar iyayen nasu dan ba yau suka saba gani ba, auta harda tsallensa duk da ba komai yake fahimta ba. Bedroom ɗin suka shiga zagayewa Lulu na dariya taƙi bari ya kamata. Cikin hakki da riƙe ƙugu ya ce, “ALLAH gara ki tsaya ma. Ni kikama wannan abun kamar wani ɗan daudu”.
Dariya ta sake kwashewa da shi da masa gwalo. Tuni ya sake yin kanta ta haye saman gado. Tsalle ɗaya ya cafkota suka faɗa saman gadon gaba ɗaya. Kanta ya haye yana mintsininsa. “Wayyo zaka fasamin ciki na banu na, nauyi fa gareka kamar Shari’a wlhy.”
“Sai dai ya fashe kuwa yau ba dai ni kikama kitso da kwalliya ba”.
“To bagaka nan ka fito a binka shar ba kamar wani ƴar budurwa. ALLAH da kai mace ne da su aunty Bilkisu sunci kuɗin samari”.
Cikin ɗage gira ya ce, “Sai kuma akai sa’a a namiji nazo ko. ALLAH kin gama da ni. Kigafa yanda yaran nan suke dariya. Yanzu wannan autan naki mai bakin surutu zai je yana bazani”. Ya ƙare maganar cikin shagwaɓa.
Dariya Lulu ta sake kwashewa da shi harda hawaye. Yayinda shi kuma ya zuba mata ido yana sake ƙwaɓe fuska. Kan nasa ta rungumo a jikinta cikin son sassauta dariyar tata take faɗin, “Sorry Babyna bazan sake ba. Ammafa ALLAH kayi ƙyau. Dan ALLAH ka yarda kullum na dinga maka kwalliya, kitson nan kuma ka barshi ai ba haramun bane ba dai tunda MANZON ALLAH ma kai ka faɗa min yanayi, mu dan ba al’adarmu bace ba dai shiyyasa idan mukayi lissafin baya dai-dai”.
“Anƙi ɗin” ya faɗa yana ture mata hannu da sauka a jikinta ya koma gefe yana faman kumbura fuska shi a dole yayi fushi. Dariyar ta sake kwashewa da shi ta tashi ta koma kusa da shi ta rungumesa ta baya. Da ƙyar ta iya haɗiye dariyar ta ce, “Sorry Babyn Baby luv ɗinsa.”
“Ban yarda ba, har zuciyarki ne?”.
“Eh mana, ai kasan ni da kai bata ɓaci”. Ta faɗa tana kai masa kisses. A hankali ya lumshe idanunsa da kamota ya juyota ta dawo saman cinyarsa. Cikin wani irin narkakken kallo da sauke murya ya ce, “I love you so much FURAR DANƘO na”.
“I love you too babyn baby luv. Amma kai ne FURAR DANƘO ba Mawaddat ba. Su Umma sun shekara sunan damawa har suka bar duniya baka zame musu farau-farau ba”.
“Ina ban yarda ba Baby luv. Ke da Daddy kune FURAR DANƘO har su Sulaiman suka faɗi baku zame musu farau-farau ba. Amma ni Ummah ai sanadin alkairi tamun, dan maybe da bata min abinda tai ba da ban zama driver na haɗu da Mawaddatan’warahmah Isma’il Ibrahim Jiƙamshi ba. Ke dai i love you irin mara ƙarewa ɗin nan har a cikin aljanna”. Ya ƙare faɗa yana wani ƙanƙameta a jikinsa ƙwalla na ciko masa ido na farin ciki da jin tamkar ya haɗiyeta. Itama ƙanƙamesan tayi tana hawaye. Kara rungumeta yay ajikinsa yana murmushi ya ce, “Kinsan abinda yabani mamaki kamar yanda su *NAWAFF* suka samu rashin jituwa atsakaninsu karshe ya rikiɗe ya koma soyayya sai gashi muma hakan ce ta kasance agaremu *RASHIN SANI* yasa muka zurfafama junanmu ƙiyayya amma ni nayi tunanin *WUTSIYAR RAKUMI* ce tayi nesa da kasa ne, ban taba tunanin zan sameki ba, na ɗauka aneman aure ma ana nuna *SIYASA KO KABILANCI*”.
Ƙara gyara zamanta tai ajikinshi tana murmushi ta ce, “Ni kaina bantaba tunanin akwai yuwuwar aure atsakaninmu ba ganin irin *TAKUN SAKAR* Daya dinga shiga tsakaninmu, sai dai da yake ance *RAINA KAMA* kaga gayya, niba abinda zance sai dai in kara godema ALLAH daya mallaka min kai amatsayin miji kamar yanda *ABDUL MALEEK* (bobo) yayi, kuma ina kara godewa ALLAH daya baroni daga rayuwar *BAKAR INUWA* wacce gwanda rana da ita, kuma gwanda ni tawa rayuwar da irin rayuwar da zaka kasa tantance *KANWAR UWACE KOH KISHIYAR UWA*”.
Kallanta yay ya ce, “Wannan ai ba *SABON AL’AMARI* bane in kikai duba da irin yadda mutanan yanzu suka kware da *SARAN BOYE*, sai dai sun mance shi *CIKI DA GASKIYA* wuƙa bata huda shi, kuma gwanda irin rayuwar da kikayi da wacce mutane suke jefa kansu *A SANADIN BIKIN SALLA*”.
kallan shi tai itama cike da shauƙi ta ce, “Toh ai kasan su mutane basu *GUDU DA WAIWAYE*, sun manta cewa *MAKAUNIYAR KADDARA* duk inda kai tana tare da kai kamar yanda *NIDA AMINIYATA** aka haɗa baki da ita don amin fyade sai dai ta manta shi *KWAI CIKIN KAYA* wahalar fita gareshi, kuma shi *KUKAN KURCIYA* jawabine me hankali kadai ke iya ganeshi”.
Murmushi yay yana shafa kanta ya ce, “Kamar yanda nima aure na dake nake masa kallan *AURAN KADDARA KO BIYAYYA* a lokacin nayita tunanin naƙi amincewa saina tuna da irin wahalar da star din littafin *BAN SAKETA BA* yasha, shi ahakanma bai saketanba saboda rabuwa da abinda kake so balai ne wanda yafi *KARAYAR ARZIKI* zafi kidaina tuna abinda ya wuce domin duk wata *DAUDAR GORA* ciki ka shata”.
Ƙara faɗaɗa fuskar ta tai da wani murmushin tace harkasa na tuna da irin soyayyar da Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul majeed Shahan-Shan na daular ruman yake nuna ma Fareedah Iffah, duk da alokacin suna cikin fuskantar tashin hankali da matsaloli, sai dai *MUTUM DA DUNIYARSA* ya dace ya gyara kansa.”
Murmushi ya sake saki mai sanyi wanda ya kara fidda ainahin kyan fuskarshi yace duk da irin tarin kaunar da yake mata bata kai kwatan kwacin wacce nake miki ba domin kedin *FURAR DANKO* ce ashekara ana damu ba farau farau”.
“Tabbas na yarda da irin son da kake min domin da *BABU SO* ba abinda zai kawo kishi Babyn Baby luv” ta ƙare maganar da manna masa kisses shi kuma yana lumshe ido da sake ƙan ƙameta. A haka yaran dake laɓe suna leƙensu da saurarensu suka shigo da gudu suma suna faɗin “Maah-maah!! Papa!! I love you so much.”✍️
*_Kai to nimafa I love you ɗin nan irin trillions wujiga-wujiga manya-manya nan masoyan amana🤣😂👏_*
*_ALHAMDULLAHI YA RABBI👏😭_*
_ALLAH na gode maka daka kawoni wannan rana ta Friday/10/2023. Abinda nai kuskuren rubutawa ALLAH ka gafarta mini kuma da kuka karanta ya gafarta muku. Sannunku-sannunku da ƙoƙarin haƙuri kuma. ALLAH ya saka muku da alkairinsa ya bar zumunci. Yanda kuka so ni domin ALLAH ina fatan kuma UBANGIJI ya soku haka ku da zuri’arku baki ɗaya. ALLAH ya karemu ya tsaremu baki ɗaya. Ya sanya albarka da tarin alkairi a garemu. ALLAH ka gafartama iyayenmu da duk al’ummar musulmi da suka rigamu kwanta dama. Marasa lafiyarmu ALLAH ka basu lafiya. Masu ciki ALLAH ya saukesu lafiya. Ƴammata da zawarawa ALLAH ya baku mazaje na ƙwarai da sukafi mazan novels ƙayatarwa da nagarta. Mu da muke gidajen auren namu ALLAH ka cigaba da bamu zaman lafiya. Masu neman haihuwa ALLAH ka basu idan alkairine, idan ba alkairi bane ALLAH ka musanya musu da abinda ya fita alkauri. ALLAH ka shirya mana yaranmu, wanda suke shaye-shaye ALLAH ka yaye musu. Masu tasowa da basayi UBANGIJI ka cigaba da kare mana su. Ya rabbi ka kawo ma musulmanmu dake cikin wani hali a ƙasashensu mafita, ALLAH ka karya azzaluman kafirannan. Ya rabbi ka kawo ma bayinka ɗauki na halin da suke ciki.😭😭👏_
*Duk wanda naima kuskure a yayin rubuta littafin nan ya yafe min dan ALLAH. Dan zata iya yiwuwa wannan shine littafin Bilyn Abdull na ƙarshe a duniya. Zaku iya jin saƙon mutuwata akoda yaushe. Idan hakan ta kasance kumin addu’a da neman gafarar UBANGIJINA dan ALLAH 😭😭🙏*.
Ta ku ce dai har kullum.
Bilkisu Ibrahim Musa (Bilyn Abdull ce😘🤳)
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,…..GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*