06/12/2019 à 14:41 - Les messages envoyés dans cette discussion et les appels sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations. 18/05/2020 à 13:43 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 *Labarin nan ya faru a gaske, sai dai a wurare daban daban, amma na canza garuruwa da sunaye, domin tak'aitawa kar gidajen suyi yawa yasa zan had'a labarin a gida d'aya.* *Nagode da gudummuwarku gareki* _Bismillahir rahamanir rahim_ _1_ Kamar saukar aradu tsohuwar nan ta d'aga hannu ta gaure matashin saurayin dake gabanta da mari, cikin d'aga murya da b'acin rai ta nuna shi da yatsa tana fad'in "Wallahi ko zaka mutu ba zan tab'a bari ka auri karuwar nan ba, *Junaid* ko ubanka dana haifa bai isa nace ga yanda za ayi ba yace a'a bare kuma kai daya haifa, in zaka auri wacce na zab'a maka ka aura, in kuma ba haka ba to ka sani zaka mutu a matsayin wanda bai b'ata aure ba har abada." A hankali ya d'ago daga sunkuyar da kan da yayi tare da d'auke hannunshi akan kumcinshi ya kalleta, kyakyawa ne sosai wanda ya had'a komai da komai, abun mamaki kuma shine wasu matasan guda biyu dake tsaye daga bayanshi wanda suke matuk'ar kama, sai dai kaman wad'ancen matasan tafi k'azanta matuk'a da alama ma 'yan biyu ne, cikin ladabi yace "Hajia kiyi hak'uri idan abinda zan fad'a zai b'ata miki rai, amma a gaskiya ina son *Maryama* kuma ita nake so na aura, Hajia munyi iya k'ok'arin mu wajen yi miki biyayya, mun bar abinda muke so saboda ke, na zama malamin makaranta ba dan raina na son haka ba, amma a gaskiya yanzu abune da zaiyi wahala, dan magana ce ta aure, rayuwa ce da ake saka rai idan har anyi to sai mutuwa ce zata raba, kenan taya zamu yarda mu auri wanda ranmu baya so? A gaskiya ni dai ba zan iya ba, kuma iyayena sun amince na aure ta haka ma Alhaji ya amince." Wuyan rigarshi ta finciko ta tilasta mishi kallon fuskarta tace "Junaid ni kake kallo kake fad'awa wannan maganar, to ka sani ni ce shugabar gidan nan sai abinda nake so akeyi, daga kai har uban naka zan iya tsine muku albarka idan kuka ce wannan yarinyar zaku shigo min da ita a cikin gidan." Sakin rigarshi tayi har saida yayi baya amma ya tsaya cak yana kallonta, gyara tsayuwarshi yayi yace "Shikenan, tunda haka kika ce ni zan bar gidan nan naje can na auri wacce raina yake so, kuma wallahi..." Bai k'arasa ba mahaifiyarshi *Zeinabu* ta d'auke shi da wani sabon marin tana fad'in "Kayi mana shiru anan." Sake dafe kunci yayi yana kallonta da mamaki, ita ma kallonshi tayi duk da tana goyon bayan wacce yake so ya aura, amma dole tayi haka saboda k'arshe abin kanta zai koma, da yatsa ta nuna mishi k'ofar fita tace "B'ace min da gani, kuma kar na sake jin motsinka a gidan nan idan bani na neme ka ba." Ya juya zai fita wata kyakyawar tsohuwa wacce fuskarta ke d'auke da tsaga wacce ake caccakawa sai tayi bak'i ga kumatu da kuma gefen bakinta, cike da dattako tace "Kai Junaid, zo nan, ba kamata yayi ya fita ba, mafita ya kamata a samu a game da matsalarshi, ba wai mu barshi haka ba." Mahaifin Junaid d'in wanda suma na gani su biyu duk kamarsu d'aya, kuma abin sha'awar ba zaka ce sun haifi kamar wannan zargadan zargadan matasan ba saboda yanda suke tsaye da kyau zaune da kyau, saidai mahaifin Junaid d'in jikinshi yafi murd'ewa kasancewarshi *soja* a cikin sojojin ma *colonel* ne, kamar baya son magana saboda yanda yayi maganar yace "Ku barshi ya tafi kawai tunda saiya mana rashin kunya ne zamu yarda da k'udirinshi." *colonel Hussein Suley Hassan Gaga* kenan wanda ko wajen aiki akafi kiranshi da Hassan Gaga. Mai kama dashi ne sak mai sunan *Hassan* wanda shine babba yace "A'a d'an uwa ba ayi haka ba, ya kamata a tattauna a tsanake dan duk yanzu kowa zuciyarshi tafasa take." A harzuk'e kyakyawar tsohuwar nan wacce kallo d'aya zaka mata kasan asalin buzuwa ce tace "Babu wani tattaunawa da za ayi game da maganar nan, na gama magana dan haka babu buk'atar sake taso da ita, ba zai tab'a auro karuwa ya kawomin a cikin zuri'a ba." Tana fad'in haka ta wuce zuwa inda zai sadata da nata d'akin baccin kasancewarsu a babban falon gidan, sai lokacin kad'ai wani santalelen tsoho dake zaune yana kallon kowa ya bita da kallo da wani murmushi a fuskarshi, uwayen ma duk barin wurin sukayi rai a jagule, tsohon kad'ai ya rage sai matasan nan guda hud'u, Junaid ne ya juya zai fita tsohon yace "Junaid, kaje ka ci gaba da k'ok'arin samun yardar Maryama, zaka aureta, wannan alk'awari na ne gareka, kaji ko?" Da murmushi a fuskarshi yace "Nagode Alhaji, Allah ya saka da alkairi." Juyawa yayi ya kalli yan uwanshi, cikin farin ciki biyu suka rumgume shi sai d'aya da yace "Ko ba komai zakayi bacci cikin farin ciki, nima Allah yasa ta amince da zab'i na." Murmushi sukayi sosai sai Junaid d'aya rad'a mishi a kunne "Ai kai ahalinta ce kake so, zata amince da gudu ma, idan bata amince ba ka mata bore irin nawa." Dariya suka sake sakawa sai d'aya daga ciki daya juya ya kalli wanda ke zaune yana latsa wayarshi alamar shi duk matsalolin nan ko a kwalar rigarshi, girgiza kai mai matuk'ar kama da shi yayi yace "Yanzu yaya *Ammar* kai ko ka tayashi farin ciki ma." Tabbas saurayin da gani kasan akwai shan k'amshi da d'acin rai da kuma miskilanci, dan ido kawai ya zuba mishi ya kalleshi take kuma ya d'auke ya ci gaba da abinda yake, d'aya saurayin ne yace "Kunga barshi da halinshi, watak'ila allurar sojojin ce ta motsa." Yana fad'a sai kawai suka kwashe da dariya harda Alhaji dake shirin tashi, wannan kuma abun shi ya tunzura Ammar ya ji kamar ya rufe su da duka, tunda iskanci ne suke mishi, sunfi kowa sanin baya da buri a duniya daya wuce ya ganshi a matsayin soja mai kare k'asar shi, amma tsohuwar can ta bakinshi ta hanashi cika burinshi, ta tilasta mishi zama likita abinda sam baya birgeshi ma a tsarinshi, amma sun samu abin tsokanarshi da shi dan sunga yana mutuwar son zama sojan har yanzu, hararan daya musu da jajayen idonshi yasa su shiru sai *Amar* wanda shine tagwaicin haihuwarshi yace "Kunga mu bar gidan nan dan ran sojawa ya fara b'acewa, yanzu ne allurar zata motsa a huce kanmu." Nan ma wata dariyar suka saka wacce tasa shi tashi da hanzari ya bi bayansu, ai da gudu dukansu suka fita kamar yara k'anana, rige-rigen fita sukeyi a bakin k'ofa hakan yasa yayi nasarar rik'o rigar *Jibril* wanda yake jika ne ga k'anwar kakansu *Husseina*, duk da kasancewar Jibril namiji saida idonshi sukayi ja kamar zaiyi kuka saboda wata matsa daya mishi a ciki ya had'a da fatar jikinshi, k'ara ya saki ya kalli su Amar da har sun kai k'ofar gida cikin muryar wahala yace "Kai dan ubanku ku zo ku taimaka min, ba tare mukayi tsokanar ba." Dariya Amar harda yin zaune k'ofar gidan yana rik'e ciki saboda ya ga k'eta, Ammar kam sosai yake sake matse mishi fata yana fad'in "Gobe ka sake min iskanci?" "A'a wallahi, daga yau gaisuwa ce tsakaninmu da kai, kayi hak'uri dan Allah yaya Ammar." Jinjina kai Ammar yayi yace "Oho, kenan yanzu ka tuna da nine yayanka ko? D'an iska kawai gobe ka k'ara." Ya fad'a yana tura shi, Junaid na ganin haka ya haura ta kan Amar dake zaune yana dariya ya fita a gidan, dukansu baya suka rufa mishi shi kuma Ammar ya juyo ya dawo ciki. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Alhaji na tashi daga nan d'akin baccin tsohuwar nan ya shiga, zaune ya sameta cikin tsananin damuwa, sam bata san ya shigo ba har saida yace " Duk wannan damuwar akan maganar auren ce?" Da sauri ta kalleshi, tana ganinshi ta ja k'aramin tsaki ta sake kawar da kanta, shi kam ko a jikinshi dan ya ga fiye da haka ya kuma yi hak'urin fiye da haka, dan haka ya d'ora da " *Zeeya'atu*, tsawon shekaru hamsin da bakwai da aurenmu, na saka miki ido kina juya yaran nan yanda kike so, dayawa daga cikinsu suna rayuwa babu farin ciki saboda kin tauyesu ta wani fannin, hatta aikin da sukeyi duk ke ce kika zab'a musu shi haka ma matan da suka zama uwayen yayansu, akwai wanda kina kallonshi zaki san baya farin ciki da zab'in naki , amma saboda biyayya sun hak'ura suna yi, to ya kamata ki sani zmanin yayan da kika haifa da zamanin yayan da suka haifa ma'ana jikokinki ba d'aya bane, yanzu ba'a tirsasa yaro yayi abinda baya so, nasan kin fara fahimtar hakan daga yanda Junaid ya miki magana yanzun nan, da wannan nake shawartarki da ki janye wannan kud'irin na cewa ba zai auri yarinyar nan ba, dan na mishi alk'awarin zai aureta kuma babu abinda zai hana hakan." Har ya juya zai fita ta mik'e tace "Wallahi baka isa ba, indai ina numfashi a doron duniyar nan Junaid ba zai tab'a auren yarinyar dake yawon ta zubar ba, ba dai a dangina ba, sannan da kake maganar babu mai farin ciki a ciki amma ai suna zaune lafiya." Juyowa yayi yace "Babu wanda yasan abinda ke b'oye cikin duhu, ki zuba ido zakiga auren Junaid da Maryama, tunda Allah bai haramta mishi ba mu ba zamu hana mishi ba, indai har zatayi tuban gaske to wannan ba matsala bane." Cike da rainin wayo tace "Idan ya aureta ya shigo da ita cikin gidan nan harta haifa mishi 'ya'ya, ya'yan wa zamu kirasu? Kana so ace ai uwarsu tsohuwar karuwa ce suma kamar yanda Jibril ya kasance jika ga tsohuwar karuwa?" Da k'arfi ya juyo ya k'ura mata ido, zuciyarshi ce ke bugawa da k'arfi yana ji kamar ya mata bugun mutuwa, saidai kuma abinda baiyi da k'uruciya ba shiyasa ba zai iya yi yanzu ba, haka ma baya so yayi magana ta hanyar bankad'o sirrin da yake ta rik'o a ranshi tsawon wannan shekarun, murmushi ya mata yace "Hum! Tabbas ba k'arya kika fad'a ba, ki sani nata karuwancin ne ya fito fili, na wasu kuma bai fito ba watak'ila talala ubangiji ya musu su gama gurza rashin mutumcinsu." Yana fad'a ya sa kai ya fita dan fad'an su ba k'arewa yake ba, shiru tayi tare da tunanin me yake nufi da abinda ya fad'a, ta jima a haka tana wannan tunanin kafin ta d'auki gabjejiyar wayarta ta dannawa Amar kira, dan daga kallon kayan dake jikinta da yanayin shigarta da kwalliyar fuskarta zaka san tsohuwar wayayya ce ta gidan gaba, yana d'auka cikin sanyin murya tace "Jikalle kana ina? Ka fita?" Cikin gatsali yace "Me kike so kuma yanzu? Ni bana gida." Murmushi tayi har saida yaji sautinsa tace "Jikalle kuma guduna kake yanzu? Me ya sa kake haka?" Cike da k'aguwa yace "Kinga Hajia, ni na fad'a miki bana gida, sai anjima." Kashe wayar yayi ita kuma ta aje gefe tana kallon wayar tace "Allah yasa ba wajen wata shed'aniya kaje ba, amma idan ma da wani abu zan gano koma menene." ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Jibril ma yana fita bai jima ba ya dawo gida, fitowa yayi daga motarshi mai shegen kyau da tsada, cikin falon ya tunkara ya bi ta inda zai sadashi da d'akin baccin kakarshi, saman bene ya kalla inda hayaniyar yara ke tashi sunata wasa da guje guje, yana kusa da kaiwa ya tsaya cak saboda tuna wani abu daya riga ya zamar masa jiki, a hankali ya rintse idonshi yana kallon fuskar a hoton k'wak'walwarshi tare da tuna wasu maganganu da suke gigita tunaninshi, duk da idonshi rufe suke amma saida hawaye suke zubo mishi saboda tuna wasu maganganu na k'arshe da macen take cewa " *Idan fa ciki ya shiga jikina sakamakon hakan? Ya kake so nayi? Wai kai baka da imani ne?*" Da sauri ya bud'a ido ya goge hawayenshi ya d'aga kai ya kalli sama yace "Allah ka kareta a duk inda take, Allah kasa bata samu ciki ba a dalilin wauta da mahaukaciyar sha'awata ta k'uruciya." K'asa yayi da kanshi tare da fad'i a zuciyarshi "Ameen." Cikin sanyin jiki ya k'arasa k'ofar d'akin yayi sallama, amsa sallamar akayi daga cikin d'akin kuma harda muryar mahaifiyarshi, shiga yayi ya samu wuri ya zauna kusa da kakarshi yana fad'in "Mama sanunku, hira kuke ke da yar tsohuwa?" Dukanshi Husseina tayi tace "Ubanka ne tsohon, ni matsa can ka bani wuri." K'ara lafewa yayi a jikinta yace "Ina zan matsa ni da na zo miki da muhimmiyar magana." Mahaifiyarshi mai sunan *Soueba* ce tace "A k'alla ka d'auki sama da wata d'aya kana fad'a min zamuyi magana amma ka kasa nutsuwa ka fad'a min." Sosa kanshi yayi yace "Mama yau dai zan fad'a muku tunda na samu k'arfin gwiwa daga abinda Junaid yayi yau." Zaro ido tayi tace "Kai duba ka kiyaye ni wallahi, kai ma rashin kunyar zakawa mutane? To babu ruwa na ni dai, Mama ku zama shaidata." Murmushi Husseina tayi tace "To ki barshi ya fad'a mana muji me yake tafe da shi, fad'i ina jinka." Kallonsu yayi dukansu yana murmushi kafin yace "Ni fa dama ina so na fad'a muku ne nima na samu matar aure." Dogon tsaki Soueba tayi tace "Aikin banza, dama wannan maganar ce zaka fad'a." Husseina ma dariya tayi tace "Wannan wacece haka zata kwashe min wannan rigimamman mijin?" Nan ma k'asa yayi da kai cikin kunya ya kalli kakarshi ya jawo kanta yace "Zo na fad'a miki a kunne." Cikin kunne ya rad'a mata ita kuma ta bud'e baki tace "Iyeee, to kai ai duk gida ne, ah gaskiya nayi farin ciki da jin hakan." Soueba ta kalla tace "Kinji fa ke, tuwo na mai na za ayi, dan yace dai *Amna* (kamar k'anwa take gareshi saboda mahaifinta da mahaifinshi yayan wa ne da k'anwa, ma'ana ita jikar alhaji ce daya haifi ubanta, shi kuma jikan Husseina ne wacce suke ciki d'aya da alhajin) yake so." Tashi yayi ya fita wai shi kunya yake ji, ita kanta Soueba taji dad'i daya kasance Amna ce yake so ba 'yar uwar haihuwarta ba *Hamna*, duk da ciki d'aya suka rayu kuma uwa d'aya ta haifesu, amma Hamna idonta a tsaye suke ga wayewa da kuma k'awaye masu ido bud'e, mahaifiyarsu *Hadiza* bata gidan yanzu shiyasa ba wani saka musu ido ake ba sosai, har ma gwara Ammar da basa shiri da ita shine ke ci mata uwa idan tayi ba daidai ba, dan akwaita da shegen yawo kullum ita ce a tafiye gidan sabuwar k'awa, musamman da mahaifinsu ya siya musu moto, ga yawan biki na k'awaye da sauran shagulgula, dan kowane wata akwai wacce zatayi bikin k'arin shekara ko kuma murnar samun wata jarabawa a makaranta, Hamna bata saka kayan kati sai atamfa, amma wani d'inkin da zaka gani a jikinta na atamfa har gwara riga yar kantin, domin kuwa bata saka kaya inba ji tayi sun kama jikinta ba sosai, bata saka zane sai siket ko doguwar riga, haka Hamna bata fita wajen biki ko wani shagali ba tare da tayi k'arin gashi na kanti ba, ko tayi kitso ko ta saka shi hakanan, indai ba sallah take ba ko zata tafi islamiyya to baka ganinta da hijab duk inda take ko zataje, yanzu haka sun shiga ajin lycée shekara biyu data wuce, rawar kanta da rashin kunyarta yasa basa shiri ko kad'an da Ammar, tana da rashin kunya da fitsara da mayar da martani, shi kuma baya d'auka hakan yasa yake mata dukan mutuwa inya samu dama, dan in mahaifiyarsu ko mahaifinsu na nan basa bari su ke d'aure mata gindi, domin kuwa a hannunsu suka tashi tun suna k'anana sosai, hatta filin sada zumunta na ahalin *Gaga* da aka bud'e akafar sadarwa ta WhatsApp Ammar fita yayi saboda Hamna kawai, saboda ko hira ake muryarta ce tafi ta kowa fitowa, ga tsokanar mutane wanda ya girmeta da wanda ta girma, ga yawon turo hotuna na sallama daban na barka da rana daban na barka da dare daban, shiyasa ranshi ya b'ace ya fita saboda haushinta yake ji sosai, duk abubuwan nan da Hamna ta had'a sab'aninsu ne ke ga Amna, dan ita ko magana ma bata cika son yi ba, ba tada kwarmniya ko kad'an, dan inma Hamna ta tsokaneta sai dai tayi banza da ita, to fa da wannan ne yasa ko murmushin Ammar baka gani a gidan, ga haushin hana shi aikin da yake so, ga takaicin rashin kunyar da Hamna ke mishi in tana cikin mutane. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Junaid na barin nan wajen masoyiyarshi ya nufa inda yasan zai iya ganinta, tun daga wajen masallacin ustaz Sani d'an jatau yake baza ido amma shiru harya k'arasa bakin *pacific*, wani lungu ya shiga da motar dan yasan suna zama nan ita da k'awar ta, amma rashin sa'a bai samu ganin ko d'aya daga ciki ba, kiran wayar k'awarta yayi dan Maryama bata d'aukan kiranshi tana ganin kamar yana takura mata, a lokacin sun fito daga cikin d'akinsu tana rufewa da d'an kwad'o kiran ya shigo, k'awar mai sunan *Iklima* ce ta kalleta tace "Mutuminki ne fa Mari, me zan ce mishi idan na d'auka?" Masha Allah, tabbas Maryama mai kyau ce ta gidan gaba, ga ta doguwa sosai da d'an kumari, gashi fatarta jawur da ita duk da tana shafa mai amma kasan ita ma akwai asalin farinta, akan luma-luma kumatunta kuma wasu tsage ne suka k'awata fuskar har guda bibbiyu, a take tace "Kawai ki fad'a masa bama tare dake, kar ma ki fad'a masa na fita." Zata d'auka kiran ya tsinke kuma sai baiyi gaggawar maidowa ba, hanyar gidansu ya nufo wanda ke bayan masallacin daya bari a farko, yana sake kira kuma Iklima ta d'auka tace "Barka da dare." "Barka Hajia Iklima, ya kike?" Cikin sakin fuska ta amsa da "Lafiya lau, ya yau?" Saida ya sauke ajiyar zuciya yace "Yau da dama, ina mutuniyar take? Nasan kema kinsan bata d'aukar kirana." Kallon Maryama tayi suna kan hanyar fitowa daga gida, kewayen wata mata Maryama ta lek'a ta same su zaune a d'an filin wurin suna kallon telbijin, matar ce ta kallesu tace "Mari fita zakiyi ne?" "Eh maman *Husna*, ina *Huda* take ne?" Da sauri wata yarinya da ba zata wuce shekaru biyar zuwa shida ba ta mik'e tsaye ta tunkarota, tana suwa ta rik'e hannunta tace "Mamma, yau ma fita zakiyi?" Da murmushi ta shafa fuskarta tace "Fita zanyi Huda, amma yau ba zan jima ba zan dawo kinji." Marairaicewa tayi ta k'ara matse hannunta tace "Mamma kullum haka kike cewa ba zaki jima ba, me ya sa ba zakiyi zamanki a gida ba?" Ba annuri a fuskarta tace "Saboda saina fita muke samu mu ci abinci." Hannu tasa a jakarta ta fito da dala ashirin (ba zasu gaza naira ashirin ba), bata tayi tace "Gashi kije Aminu ki siyo madara kisha, idan kinji bacci kije lungunmu ki kwanta nayi shinfid'a." Juyawa tayi zata fita taji ta rik'e hannunta, tana juyowa yarinyar tace "Mamma meyasa ke saida dare kike nemo mana abinci? Ki dinga zuwa da rana mana tunda baki komai a wannan lokacin." A hankali ta zage hannunta daga na yarinyar ta sake juyawa, kamar saukar ruwan sama ta tsinci muryar Huda na cewa "Mamma kenan da gaske ke 'yar iska ce?" Tsayawa tayi amma bata iya juyowa ba saboda hawayen da take, Iklima na ganin haka ta fice ta barta, da sauri ta taka ta barta nan ta fita, amma saboda wayo da kuma k'uruciya sai yarinyar ta fito da gudu har k'ofar gida tana kuka cikin d'aga murya tace "Ashe dama ban da uba, ni shegiya ce, to ni dai bana son neman abincin naki hakanan, daga yau ba zan sake cin abincinki ba idan kin kawo, kije kawai karma ki..." Marin da Maryama ta d'auke ta dashi yasa yarinyar fad'uwa k'asa, wani daga cikin masu zama a k'ofar gidan ne ya kama Huda ya d'auke ta yana rarrashi. Iklima dake amsa wayar Junaid shi kuma a daidai lokacin ya k'araso k'ofar gidan, cikin rashin sani tace "Mari ai tun rana rabona da ita dana barota gida, izuwa yanzu kuma nasan ta yada zango a wani wurin." Daga inda yake ya hango fitowarta sai Maryama dake bayanta, daga cikin wayar yayi murmushi yace "... *Allah ka mana kyakyawan k'arshe.*👏 18/05/2020 à 13:46 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 _Bismillahir rahamanir rahim_ _2_ Daga cikin wayar yayi murmushi yace "Karki damu ma naga hasken idaniyar tawa." Da sauri ta d'auke wayar daga kunne ta juya hagu bata ganshi, tana juyawa dama ta hangoshi yana fitowa daga motar, a hankali ta fara takawa wajen shi sai Maryama dake biye da ita a baya wacce bata san meke faruwa ba, saida taga Iklima ta tsaya wajenshi kad'ai ta fahimci mayenta ne ya sake dawowa, tsaki tayi ta tafi a harzuk'e zata wucesu kamar bata gansu ba ma, da sauri ya tare gabanta da gudu gudu, kallon juna sukayi kafin tace "Malam matsa min a hanya ko." Kai ya girgiza duk yayi kalar tausayi yace "Ba zan iya ba Maryama." Tab'e baki tayi tace "To saika zauna kayi gadin wurin ko, ai shi zaka iya na sani dan kamar kaine ka yankewa wahala cibiya lokacin da ta zo duniya." Murmushi yayi dan kalaman da suka fi wannan ma ya jisu a bakinta, zata rab'a ta wuceshi ya sake tare gabanta yace "Dan Allah Maryama ki saurare ni, wai me ya sa har yanzu idonki sun kasa gane miki masoyinki na gaskiya ne? Maryama me ya sa ba zaki yarda da soyayyar da nake miki ba?" Da k'arfi tace "Saboda duk maza halinku d'aya ne, kana son samun soyayyata ne saboda kawai kana son jikina, kuma na fad'a maka ni yanzu a ruwa nake, karuwa ce ni, ba buk'atar saika yaudareni kafin ka samu jikina, 2000f cfa (jaka biyu) kad'ai ka bani zan iya kwana tare da kai, saboda ni k'aramar karuwa ce da aka cewa *je ki kya gani*, abinci kawai nake nema da zan ciyar da kaina da kuma 'yata, tunda muma halitta ce ba zamu iya rayuwa babu abinci ba, amma kai ka tsaya sai wahalar da kanka kane kana b'ata min lokacin da rera min wani banzan wak'anka wai kana so na, mtssss." Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata k'aramin bakin, har k'asan zuciyarshi tana birgeshi, yana son kallon kyakyawar fuskarta mai d'auke da tsagu har hud'u, wanda kowane kunci ya samu bibbiyu, amma ta kasa fahimtarshi har yanzu, wani murmushi yayi mai kama da ciwo yace "Yanzu akan jaka biyu kad'ai Maryama kike wofantar da kanki ga mazan da basu san ciwon kansu ba? Maryama akan kud'in da ba zasu iya siya miki ko zanin atamfa ba kike kwanciya da duk d'a namijin daya miki magana? Maryama taya zaki illatar da kanki da gangan alhalin kinsan ba kya da kud'in warakar matsalarki ba?" Hannayenshi yasa aljihu ya lalaba ya fito da duka kud'in dake cikin ak'alla sun ba jaka d'ari biyu baya ya janyo hannunta ya damk'a mata kud'in a hannu kamar zaiyi kuka yace "Karb'i wannan kiyi duk buk'atunki iya na yau kawai, ni kuma na miki alk'awari kowace safiya zan kawo miki adadin wannan kud'in dan biyan buk'atar ki kawai data 'yarki, amma ki min alk'awarin babu ke babu sake kula wani namijin, ki bani tabbacin zaki kula min da kanki za kuma tsare min mutumcinki, dan Allah Maryama." A hankali ta raba hannunta da nashi ta sakar masa kud'in a hannunsa tana kallon cikin idonshi tace " Bana buk'atar taimako daga wajen kowa, zanyi aiki da jikina wajen samo mana halak d'in da zamu ci, amma bana son kud'in ka, kad'an d'in da nake samu sunfi min masu yawan da zasu fito a hannun kowane d'a namiji." "D'a namiji! D'a namiji! Maryama kullum maganarki kenan d'a namiji, wai wace irin ta'sa namiji yayi miki haka da har kika mana kud'in goro haka? Ki fad'a min ni kuma zan tsaya tsayin daka wajen ganin na goge waccen bak'in fantin da waccen mutumin yayi mana, sannan ki bar tunanin halak kike ci ke da yarki, kud'i ne da kika samu ta hanyar sab'awa ubangiji." Kallon idonshi tayi wanda suka cicciko da hawaye tayi wani murmushi tace "Ba zaka tab'a iya goge wannan bak'in fantin ba, kamar yanda ba zaka iya dawo min da mahaifina dana rasa ba a dalilin wautar d'a namiji irinka, haka kuma ba zaka tab'a sawa mahaifiyata ta kalli idona ba bare harta min magana irin ta uwa da d'iya, dan haka dan Allah Junaid ka rabu dani nayi rayuwata, ka barni na k'arasa k'azamar rayuwa ta a haka ba tare daka tuna min da baya ba, ina farin ciki da hakan." Murmushi ya mata yace "Magana kawai kikayi akan baya, amma gashi har na iya hango triste (damuwa) d'in da kike ciki, Maryama tu es en colère (kina cikin hushi), kamar fansa ce kike son d'auka ko kuma dai hushi ne ke sakaki abinda kikeyi." Cikin k'ok'arin b'oye damuwarta tace "Laise moi en paix (ka bani lafiya)." Wucewa tayi yabi bayanta da kallo, Iklima ce ta zo wucewa ta gabanshi ya bata kud'in nan yace "Dan Allah Iklima ki rik'e wannan kud'in kuyi wani anfanin dashi, sannan ki sanar da Maryama irin son da nake mata, wallahi ko misk'ala zarra bana da niyyar cutar da ita, aurenta nake so nayi, yau d'in nan har nayi magana da magabata na, kuma na samu amincewar kowa, ita kad'ai ta rage min na samu ta ta amincewar, na rok'e ki Iklima ki taimaka min na shawo kanta." Da mamaki ta kalleshi tace "Kana nufin ka sanar a gidanku zaka aure ta?" Cike da tabbatarwa yace "Na sanar mana." "Kuma sun amince ka ce?" "Sosai ma, wallahi da gaske nake Iklima." Ajiyar zuciya ta sauke tace "Kuma ka fad'a musu irin matar da kake son aure?" "Na fad'a musu Iklima, amma ban fad'a musu tana da 'ya ba, abu mai mahimmanci su san wacece zan aura." Zata wuce yace "Kud'in fa?" Juyowa tayi tace "Ka barshi kawai mun gode, idan na karb'a zamu samu matsala da Mari ne." Wucewa tayi shi kam yabi bayansu da addu'ar shiriya, cikin sanyin jiki kamar kullum ya shiga motarshi ya kamo hanyar gida dan babu abinda zai tsinta a wajen. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Su Hamna yan mata sune a falon sama tare da yara ta kunna wak'a a wayarta sai rawa take yaran na biyarta a baya, Amna na zaune tana kallonsu tana dariya, sai Umminsu Ammar da ita ma take kallonsu tana dariyar tare da mahaifiyar Junaid, a gefe ma k'anwar Junaid ce *Jamila* duk da ba ita ke bi mishi ba, amma ita ce daidai su ma'ana warin haihuwa, dan yayarta *Umaima* bata cika son hayaniya ba itama, tana da tsatsauran ra'ayi, ita d'in ce wacce suka zama k'awaye da ita suna ta kallonsu, wannan hayaniyar ce tasa Ammar daya dawo falon ya zauna yana danna wayarshi yayi tsaki yafi dubu, in dai yace yaje yanzu dan yayi musu magana Ummi za tace ai zai takura ma yaranta ne, kuma yana da tabbacin in yaje sai ranshi ya sake b'aci saboda *kankana* *(sunan daya sakawa Hamna kenan saboda soyayyarta da kankana*😂), su kam basu san tsiyar da yake ba sai rawarsu suke kwasa, wannan dum-dum d'in da wajen ke amsawa yasa yake jin kamar benen zai fad'o mishi a kai, wani wawan tsaki ya sake ja yace "Wannan yarinyar wallahi saina karya mata k'afa ta yanda gobe ba zata iya rawar ba ma, ayi yarinya kamar dujal ne ya haifeta, mtssss." Wasu lambobi ya danna saiga lambar Amna ta bayyana a wayar tashi, kira ya aika mata da shi ta d'auka cikr da nutsuwa da fad'uwar gaba dan ita har ga Allah tana tsoronshi, duk da akwai banbanci tsakanin Hamna da Amna mai yawa, domin kuwa Hamna na da tsoron k'ananun dabbobi irun su k'adangare, kyankyaso, tsaka dacdai sauransu, Amna kuma bata tsoron wannan halittu kamar yanda take tsoron Ammar, Hamna kuma bata da zuciya da sanin ciwon kai, dan duk maganar da zaka fad'a mata komai zafinta saira karkad'e tace ko a kwalar rigarta, shiyasa duk maganganun da Ammar ke fad'a mata bata jin zafi, sai dai kuma akwai yab'a magana ita ma, dan tsoron da Amna ke masa ita bata mishi, idan taga ta shiga hannunshi kad'ai take tsorata da razana, sab'anin Amna kuma da magana ke mata mugun zafi, tana da zuciya da hushi, a tak'aice ma dai ita masifaffiyar amma fa ga wanda ya tab'a ta, idan kuma ka ganta zaka d'auka ko hannu ka saka mata a baki ba zata ciza ba, amma idan tana fad'a ko tayi zuciya to babu kyau, cikin sanyin murya ta amsa da "Na'am yaya Ammar." Sai kace a gabanshi take saboda yanda ya wani sake had'e rai murya k'asan mak'oshi yace "Ki fad'awa yarinyar nan ta kashe mana kid'an nan, idan kuma na samesu a nan ran uban kowa saiya b'ace." Yana fad'a ya kashe kiran tare da ci gaba da abinda yake, Amna kuma kallon wayar tayi kafin ta kalli Hamna tace "To shakira ya isa haka ko tunda *boss* yace a kashe wak'ar nan, da alama kuna damunsa ne." Kallonta Hamna tayi masha Allah kam kyakyawa ne ajin farko, suna da diri da k'ira gwanin ban sha'awa, amma duk da haka Hamna tafi haske sosai da tsayi kad'an, tab'e baki tayi tace "Shine ya kiraki kenan?" Da ido kawai ta mata alamar eh, ci gaba tayi da rawarta tace "Ki kira ki fad'a masa bai isa ya katse mana jin dad'in mu ba, dan haka yanzu muka fara." *Hajia Zeinabu* (mahaifiyar Junaid) ce tace "Um um fa Hamna, hanyar lafiya abita da shekara, tunda yace ku kashe to ku kashe, ko kuma ki jasu kuje d'akin ku sai kuyi acan." Wata kyakyawar mata mai k'aramin jiki ce fara kuma doguwa ce tace "Saboda yace baya so shikenan sai a daina? Me zai hana ya fita waje tunda namiji ne shi, amma yana cikin gida kamar wata garar kunya." Zeinabu ce tace "Da dai kin basu shawara su koma ciki zaifi ai." Hamna ce ta kalli yaran tace "Kai mu ci gaba da nishad'inmu, kunsan boss ba fara'a yake ba bare maganar nishad'i, shi ya sa yake kishi da duk wanda yake yinsu." Tana maganar ne tana amma sai taga yaran kowa yayi zaune tare da mak'alewa wuri d'aya, tab'e baki tayi tace "Sai kace mala'ika nr shi daga ya turo sak'o ta waya amma duk kun tsorata." Kallonta ne ya kai kan Amna data kafeta da ido, cikin dubara Amna ta d'ora hannunta a bakinta da yatsa d'aya take mata nuni da k'ofar shigowa falon, da k'yar ta fahimci abinda take nuna mata ta juya dan ganin ko meye, ai ko ido cikin ido suka kalli juna ita da Ammar wanda yake tsaye k'ik'am ya cije gefen labb'enshi na k'asa, ai da gudu Hamna ta koma bayan Ummi tana mata rad'a wai "Dan Allah Ummi ki bashi hak'uri mu samu ya bar gidan nan." Ummi da tunda ta ganshi ta had'e rai kamar dai shi kalloshi take sosai, ganin yanda take kallonshi yasan sai ranshi ya b'ace in yayi magana, dan k'aramin aiki ne a gurin Ummi ta zageshi a gabansu har ma tayi yunk'urin marin shi, dan haka yayi k'wafa ya juya ya bar d'akin, yaran na gabin haka suka daka tsalle da shewa wai ya tafi bai dake su ba. Yana barin nan kai tsaye asibitinsu ya wuce mai sunan *Clinik Aminci*, (na canza mata suna saboda kar na saka na ainahin sunan familyn ya fito fili), yana zuwa ya fito daga mota ya tunkari shiga ciki, a babban falon da mutane ke zama ya samu duk gurin zaman an cikeshi, kuma yana da tabbacin wanda yake da rendez-vous (appointment) da su ne, wata irin sallama ce yayi wanda na farko kawai yaji shi sai wanda suka ga bakinshi ya motsa, dan ranshi b'acewa yake idan ya zo asibitin ma, a ganinshi da yanzu watak'ila yana filin daga suna bada wuta, amma an zaunar dashi yana tambayar lafiyar mutane (mutum baya sanin abinda yake, haka kuma baka sanin mahimmancin abinda ke hannunka saika rasa shi), malamar asibitin dake zaune akan babban teburi wacce ita ke kula da wanda zasu shiga da kuma fara duba lafiyarsu, kallonshi kawai tayi dan ko ta gaishe shi ma ba amsawa zaiyi ba, tsaye yayi gabanta ya sauke jajayen idonshi akanta yace "Zan shiga, su bi layi da kyau, a kuma dinga shiga da hanzari saboda gudun b'ata min lokaci." "Ok docteur." Ta fad'a tana bin bayanshi da kallo, tab'e baki tayi tana gunguni tana fad'in "Kamar dai ba *Sa'ada* ce ta haife shi, ita faran faran da mutane, shi kuma sai shegen tsamin rai, Allah ya sawak'e maka." Yana shiga ya mayar da k'ofar ya rufe, makullin mota da wayarshi ya aje akan tamk'amemen teburin dake gabanshi tare da zagayawa wajen wani d'an dogon k'arfe ya zago fara kuma doguwar rigarshi ya saka, abin sauraren numfashi ya d'auko kamar zai saka a kunnuwa sai kuma ya sagalashi a wuya, kujera ya ja ya zauna ya gyarawa abin auna hawan jini zama, wani k'aramin coffre ya bud'e ya d'auko wani farin gilashi ya saka a idonshi, masha Allah, abinka ga kyakyawa kuma farin mutum, sai yayi kyau cikin shigar kamar ka daga da bredi, matsalar d'aya ita ce d'aurewar fuskar nan da babu annuri a cikinta, wani babban littafin ya d'auka ya ciro alk'alami a jikin rigarshi ta ciki ya fara rubutu, ba jimawa da fara rubutun kuma aka k'wank'wasa k'ofa tare da bud'awa aka shigo,sam baiyi alamar yasan da zuwan mutum ba saboda ko d'agowa baiyi ba, har saida matar ta zauna tare da kafeshi da ido, saida ya gama abinda yake ya d'ago a hankali ya sauke ido akan matar na yan dak'ik'u, hannu ya mik'o mata alamar ta bashi katinta da kuma takardun rahoton lafiyarta, da sauri ta mik'a mishi saboda ita tsoro ma ya bata, saida ya gama dubawa da rubuce rubuce bai kalleta ba yace "Ki kwanta kan gadon can." Tashi tayi ta nufi wajen gadon da aka keyawa ba'a iya ganin wanda ke ciki ta kwanta, tashi yayi ya fara dubata na wasu mintoci kafin ya dawo ya zauna, dawowa tayi ta zauna ita ma tana kallonshi yana ci gaba da rubutu, ya jima kafin ya mik'o mata takardun sai takardar siyan magani yace "Wannan takardar ki bawa wannan likitar dake zaune." Wata takardar ya mik'o mata yace "Wannan kuma asiyo wad'annan magungunan yanzu, dukansu kina buk'atarsu domin zasu taimaka miki." Mayar da kanshi yayi k'asa ya fara rubuce rubuce, tashi tayi ita kuma ta fita jiki na rawa dan tayi abinda yace, da haka Ammar yake duba duk wani majinyaci daya shigo har saida lokacin tashinshi yayi, ak'alla awa biyu ya d'auka a asibitin kafin ya tattara ya nufi gida a gajiye, wasu mintuna ne suka kawo shi gida, yana zuwa kuma a k'ofar gida ya samu Hamna tare da wata k'awar ta akan moto da alama tafiya zatayi, tsaki yayi ya shige ciki kai tsaye kuma b'angarensu na samari ya wuce, tun a falon ya tarar da su Amar da su Junaid, kallonsu kawai yayi ya nufi na shi d'akin, Junaid ne yace "Likita bokan turai, baka so a mutu baka so a zauna lafiya, daga asibiti ake halan?" Tsaye yayi ya rik'e k'ugu ya kalleshi kamar zaiyi magana sai kuma ya wuce, Jibril ne yace "Oh mu 'yasu, mu dai mun shiga uku kam, jama'a namiji da jan aji da yanga kamar wata sabuwar bazawara, wannan naga mai auren shi a duniyar nan." Dariya Amar yayi yace "Za kuwa ka ganta da idonka, ai irinsu kuma Allah yake had'awa da masu shegen surutu." Karaf Jibril yace "Kamar irinsu Hamna ba." Wata harara Junaid ya wurgo masa yace "Ka rufa mana asiri kafin zaman d'akin nan ya gagare mu, yana jin wannan maganar a bakinka Allah saiya maka tiyata a baki." Dariya suka saka inda suka ci gaba da tattaunawa cikin nishad'i, amma abin haushi duk hirar dangin nan da suke Ammar na d'aki na jin hayaniyarsu yayi shiru har bacci ya d'auke shi. *Washe gari* Jiniyar motoci ce ta tashi wasu daga cikin mutanen gidan, daga ciki har da Ammar da Hamna da kuma Amna, sanin ko waye yasa Hamna ko suturta jikinta bata tsaya yi ba daga kayan baccin dake jikinta ta fito, da gudu take saukowa daga matakalar tana fad'in "Abbanmu ya zo, Abbanmu ya zo, Abbanmu ya zo." *GVR* de Maradi (gwamnan Maradi) *Harouna Suley Hassan Gaga* (Gambo) kenan, mahaifin Hamna da Amna, wanda suke kwashe watanni basu saka shi a ido ba saboda yanayin aikinshi, yanzu haka ma yayi sammakon zuwa ne sabida k'arfe *09:00* zai halarci wani taro na k'addamar da wata sabuwar gidauniya da za'a bud'e, shiyasa ya zo dan ya samu ko da awa biyu ne da iyayenshi, 'ya'yanshi wanda yan uwanshi ke kula dasu da kuma sauran 'yan uwa, kuma bayan rabuwarsu da mahaifiyar su Hamna ya auri wata mata mai sunan *Salamatou*, yar asalin garin Niamey ce bazabarma (zarma), suna tare da ita acan babban birnin niamey, shiyasa ganinshi ma ke zama aiki, dan ko a waya ka kirashi sai ka taki sa'a kake samunshi. Masha Allahu, gaskiya 'yan biyu akwai kyau kuma kyauta ce ta Allah, uwa uba kuma 'yan uku, cikin d'an takon hanzari yake shigowa falon tare da yi wa masu tsaron lafiyarsa alamar su jira shi, Hassan da Hussein da suka fito cikin shirin fitarsu kowane da kayan aikinshi ne ke tunkarowa suma saboda ganin d'an uwansu rabin jikinsu, sak iri d'aya su ukun, kayan jikinsu ne kawai ya banbanta su, sai dai kuma shi Gambo ya d'an fisu kumari, ganin irin farin cikin dake kan fuskokinsu yasa ya yanke shawarar k'in fad'a musu abinda ya kawoshi, zaiyi shiru har kowa ya gama tafiya wajen aikinshi, kafin su dawo kuma yasan ya bar garin, rumgume juna sukayi dukansu saboda farin ciki, ba jimawa suka raba jikinsu suna kallonshi, Hassan ne ya d'an bugi tunbinshi yace "Meye haka kai kuma? So kake ka zama luti ka barmu, wato kana so a dinga cewa kaine babba garemu ko?" Murmushi yayi ya gyara babbar rigarshi ta shaddarshi ruwan madara wacce ta dace da shi yace "Ai babba babba ne, kaifa ka fara zuwa duniyar nan kafin mu, kaga kuwa dole mu baka girmanka." Cikin had'add'en fuskar da babu annuri Hussein dake gyara d'amarar shi ta kakinshi na soja yace "Girman guda nawa ne, ko na minti biyar fa bai kai ba." Kallonshi Hassan yayi ya kai hannu yana k'arasa sakawa Hussein d'in mab'allan rigarshi kamar wani yaro yana fad'in "Soja mazan fama, ai ka ma rik'e girman nawa na bar maka." Dukansu ne suka juya saboda muryar Hamna dake kiran Abbanmu ya zo suka kalleta, ganin riga da wando ne a jikinta na bacci yasa Gambo daka mata harara har yana mata nuni da yatsa yace "Maza kije ki canza kayan nan, wai ke yaushe zakiyi hankali ne?" Cak ta tsaya tare da turo baki gaba, juyawa tayi harda bubbuga k'afa ita bata so ba, Hassan ne yace "Daga zuwanka fa ba zaka fara takura min 'ya ba." A lokacin Hussein na gyara zaman jar hularsa mai d'auke da lambar girma yace "Idan ya takurata ka kira ka fad'a min, zan nuna maka inda nake ajiyar bindiga ta." Yana fad'a yasa kai zai nufi d'akin Hajia dan gaisheta cikin wani irin tako kamar wani ingarman doki, (ni fa sai lokacin ma na ce duk d'abi'un shi kamar Ammar, ko kuwa Ammar d'in ne kamar shi) da sauri Gambo yace "Ina kuma zuwa bayan na zo?" Ko juyowa baiyi ba yace "Zuwanka kuma ba zai dakatar dani daga tafiyar nan da zanyi ba." Wata tattausan murya ce daga bayansu aka ce "Yallab'ai ga shayin." Hassan ne ya juyo ya sauke idonshi akan kyakyawar matarshi, hannu yasa ya karb'a yace "Nagode uwarsu Ammar." Murmushi ta sakar masa mai tsadar gaske tare da kallon Gambo tace "Sannu da zuwa gwamna, ya hanya?" Da fara'a ya amsa mata da "Alhamdulillah madame, ya muka same ku?" "Lafiya lau muke? Ya mutan can d'in?" "Lafiya lau, ya 'yan rigamarki (su Hamna ba)?" Murmushi tayi tace "Yara na ai sun girma yanzu sun daina rigima." "To zan gani dai, dan banga alama ba sai dai ko Amna." Hassan ne ya mik'a mata kofin shayin tare da karb'ar hularshi kalar shud'i ya d'ora akai ya daidaita mata zama yanda a dace, (ikon Allah, idan dai na fahimci wani abu wato duk gidan nan boko ce ta yanke musu cibiya, lallai wasu kayan sai amale), *lieutenant Hassan Suley Hassan Gaga* babban douane na garin Maradi, murmushi ya sakar mata yace "Mu zamu fita kuma sai Allah ya mana dawowa." Murmushi ita ma tayi tace "To muje na raka ka ko, ko ba kya son addu'ar tawa yau?" Murmushi yayi daya bayyanar da hak'oran shi yace "Zan iya hak'ura da tenue (kaki) na amma ba dai addu'ar ki ba." Wucewa sukayi ya dafa kafad'ar Gambo yana fad'in "D'an lukuti saina dawo." Murmushi kawai yayi yace "A dawo lafiya, madame ke ba zaki tafi wajen aikin ba yau?" Juyowa Hassan yayi yace "Ai saita fara iza k'eyata gaba take tafiya." Dariya sukayi suka fice shi kuma ya nufi d'akin Hajia dan ya fara kai mata gaisuwa, Hamna ce ta sake fitowa ta d'oro hijab akan kayan baccinta sai Amna a bayanta, kallonsu yayi da sauri Amna tace "Bonjour (ina kwana) Abba." "Bonjour." Ya fad'a yana tafiya ya d'ora da "Attend moi ici (ku jira ni anan), je salut mes parents (zan gaida iyayena)." Amna ce dai ta amsa da "Ok Abba." Yana isa a lokacin kuma Hussein ya fito, sallama ya mishi ya fito da zuwan saiya dawo, ganin su Hamna zaune a falon yasa ya kallesu yace "Yarana ya dai?" Gaishe shi suka fara yi, kafin suce wani abu kuma Ammar ya shigo ba sallama, hasalima fuskarshi had'e take saboda yaga kankana a wurin, amma yana ganin kawunshi sai kawai ya k'ame wuri d'aya tare da sara masa wai shi a dole soja ne, shi ma colonel d'in sara masa yayi tare da dafa kafad'ar shi yace "Bien réveillé (ka tashi lafiya)?" Cikin k'amewa irin ta sojoji ya amsa da "Oui chef." Kamar wanda suka had'u a filin daga haka shima colonel d'in yace "Da kyau, yanzu kaje ka fara da motsa jiki, kar ka ci abu mai nauyi sosai, sai ka wuce wajen aiki, compris (ka fahimta)?" Da k'arfi ya amsa da "Tout de suite (yanzu kuwa) chef." Sai lokacin ya saki jikinshi tare da d'an fad'awa jikin kawun nashi suka yi gaisuwa cikin nutsuwa, sai lokacin yace "Tonton (kawu) na d'auka hutu ka zo mana ai, ya kuma zaka fita yanzu?" Ba tare daya saki hannunshi da sukayi musabaha ba yace "Ba jimawa zanyi ba, wani taro ne zanje anan *gazawa*." Ba karsashi yace masa "Saika dawo tonton." Fita yayi daga falon ya wuce inda zashi, Ammar kuma juyowa yayi inda su Hamna suke zaune, ai yana kallonsu sai kuwaHama ta bushe da dariya, Amna baiwar Allah tana so ta dara amma ba dama, k'ara tsumimiye fuska yayi yana kallonta baice komai ba, ita ko dariya take shek'awa kamar zararra harda tashi daga kan kujerar ta koma bayan Amna tana fad'in "Oui chef, hhhhhhhhhh, tout de suite chef, wayyo cikina harya k'ulle, yer uwa." Ta fad'a tana tab'o Amna ta ci gaba da fad'in "Allah dai wani ya zare a gidan nan saboda bai samu abinda yake so ba, kullum shine fad'in, oui chef, a vos ordres chef, caca-caca, kai haba ina." Kwabar dake gefenshi ya kallasai kuwa yayi sa'ar samun faranti na tangaren, d'auka yayi ya saita daidai kan Hamna zai jefa sai kawai kawunshi Gambo ya fito tare da Hajia da kuma Alhaji, sauya akalar farantin yayi cikin dubara ya aje shi mazauninshi, Hamna na ganin haka ta mishi gwalo tare da kwaso wata shegiyar shoki ta watso mishi a fuska tana fad'in "Eh, eh-eh-eh shokiii." K'wafa yayi a zuciyarshi kawai ya juya ya bar d'akin, lokacin kuma Hajia Husseina da Soueba suka fito tare suma, da haka har falon ya sake cika da iyalin Gaga yara da manya, saidai kowa yana haramar tafiya sabgar gabanshi ne, yara da matasan école (school) suka nufa, sai samarin dake fitowa cikin nasu shirin tafiya ma'aikatunsu. Hamna da suka saka mahaifinsu tsakiya sai shagwab'a suke masa, Ammar da Amar ne suka shigo tare, k'are musu kallo Hamna keyi tana son banbance boss da kuma Amar a ciki, dan dukansu riga ce chemise a jikinsu kuma fara k'al, kuma dukansu basu b'alla botira biyu ba na sama, haka ma wandon jikinsu mai duhu ne sai dai ba kala d'aya ba, zaka fahimci hakane idan sun matso kusa da kai, sannan takalmin k'afar su iri d'aya ne da kuma gilashin idonsu fari mai kyau, a ciki ba zata iya cewa ga boss ba dan bata gama fahimtar Ammar ne ya saki fuskarshi ko kuma Amar ne ya had'e rai kamar boss, cikin takonsu na zataran maza majiya k'arfi suka k'araso kusan kawunsu, mik'ewa yayi tsaye suka rumgume juna da su cikin farin ciki da k'aunar juna, saida suka raba jikinsu Gambo ya kallesu da kyau yace "Yaran nan raina min hankali zakuyi ko? To a ciki ina Ammar?" Wani ikon Allah sai kawai Amar ya d'an saci kallon Hamna lokaci d'aya kuma ya d'auke kanshi, ai kuwa Hamna sai cewa tayi "Abba ga boss nan." Ta fad'a har da nuna shi da yatsa. Tare suka kalleta amma tana had'a ido da Ammar d'in sai taji gabanta ya fad'i da k'arfi, Gambo ne yace "Waya saka dake?" Turo baki tayi shi kuma ya sake kallonsu sai Ammar daya matso kusanshi yace "Tonton." Murmushi yayi yace "D'an soja ya aikin na ka?" Cikin gimtse hak'ora ya amsa da "Pa mal (ba wuya) tonton." Kafin yace wani abu ya sake cewa "Tonton je dois mon aller (ina so zan tafi), j'ai une visite dan quelque minute ( ina da wanda zan gani nan da 'yan mintuna)." Kafad'ar shi ya dafa a lokacin Amar yace "Amma dai tonton zamu sameka gida ko?" Kallonshi yayi yace "Pourquoi tu demande ça (me ya sa ka tambaya)?" Kallonshi shima yayi yace "Parce que hier j'ai reçu une carte d'invitation en fecebook dans mon counte (saboda jiya na samu wani katin gayyata a fecebook a ma'ajiyata), ce pour cela je demande (shiyasa na tambaya)." Kallonshi kawai gwamna yayi dan ba zai iya cewa ba haka bane, sai Ammar daya kalli Imminsu wacce ke cikin shirinta yace "Ummi yau ba zaki fita asibitin bane?" A tak'aice ta amsa da "Ina bayanka." Kallon gwamna yayi yace "Tonton sai mun dawo." "Ok yarana, Dieux vous bénisse (Allah ya muku albarka)." Saida suka sunkuya suka gaishe da Alhaji da Hajia wacce ta hakimce kai kace wata matar gwamna ce, ta tsufa amma bata jin ta tsufa saboda ta tilasta yara suna yin aikin da take so, kowa ya ji k'ara (alerte) a counte d'in shi ita ma sai taji, ko sutura da take sawa kawai ya ishi gidan wasu cefanai na tsawon wata d'aya, saboda k'arfin hali waya ma cewa tayi sai babba take so wanda ake shafawa da hannu, shiyasa in ka kalleta kallon garaje ba zaka fahimci tsufanta ba, yanda Ammar ya gaisheta ne yasa ta yamutsa fuska ta kalleshi tace "Da ka rik'e gaisuwar taka ai, idan baka sunkuya ka gaisheni ba to ubanka har k'asa zan sashi ya duk'a ya gaishe ni, kuma bai zama lalle na amsa ba, imbécile kawai." 😂 *(Romo kenan)* Ammar kuma da dama shi dai yake jin haushin hana shi abinda yake so da tayi shiyasa basa shiri, juyawa yayi zai wuce ya kalli Ummi data mik'e ita ma, daf da ita ya matso zai wuce ya fita murya k'asa k'asa tace "Ban yafe maka ba in har baka gasheta da kyau ba." Cak ya tsaya tare da cije leb'e da k'arfi, shi dai ya rasa wace irin rayuwa ce wannan, komai k'ank'antar abu sai Ummi tace ban yafe ba, k'wafa yayi cikin zuciyarshi ya sake juyowa yaje gabanta, zai sunkuya ta d'aga mi shi hannu tace "Wallahi ka durk'usa saina tsinkeka da mari a wurin nan, ni zaka rainawa hankali, in tsuguna in haifi ubanka amma kana jin haushin gaisuwar fatar bakin da zaka min wai har sai uwarka ta saka ka, kenan albarkacinta na ci? To bana so ka rik'e tsiyarka, amma ka tambayi ita kanta uwar taka, ta shigo gidan nan ne saboda ni na zab'i ta shigo, sannan tana zaune a gidan nan ne har yanzu saboda ina so, kuran waya d'aya tak ya isa ya jefa uwarka a layin zawarci." Ammar dake tsaye zuciyarshi sai bugawa take, hannunshi na dama sai rawa yake yana ji kamar ya kai mata haura guda, k'ara damtse leb'en shi yayi sosai ya kalleta da jajayen idonshi, a hankali ya d'auke idonshi ya kalli gefenta sai kawai Ummi, k'wayar idonta ya kalla ya ga sun cika taf da hawaye, da ido ta mishi alamar "Hankalinka ya kwanta yanzu?" D'auke idonshi yayi yana ji kamar ya k'urma ihu, tafin hannunshi yasa ya dafe goshinshi yana d'an murza idonshi da yatsunshi ta k'asan gilashin shi, saida ya sauke ajiyar zuciya har sau uku kafin ya sake kallon Hajia, zai kuma durk'usawa dan bata hak'uri cikin tsiwa tace "Na fad'a maka wallahi saina mareka idan ka durk'usa gabana." D'ago kai yayi daga shirin sunkuyawar ya sauke a kanta, a ranshi yace "Wai ni ya zanyi da tsohuwar nan ne?" Ummi ya kalla danya nuna mata shifa ba zai zauna anan ya b'ata lokacin shi ba, sai yaga har yanzu wannan kallon ne take masa, ya kuma sani ita ma yanzu in suka je asibiti abinda zata mishi kenan, wani k'aramin tsaki yaja wanda bai ma san ya fito fili ba, muryar Alhaji ta dawo dashi yana fad'in "... *Tsaka mai wuya Ammar (ka sunkuya Hajia ta mareka, ka k'i sunkuyawa Ummi tace bata yafe ba).* _Ku bashi shawara_😂 18/05/2020 à 13:48 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 _Bismillahir rahamanir rahim_ _3_ Alhaji ne yace "Kai Ammaru, wuce dan Allah ku tafi wajen aikinku kaji, sai kun dawo." Da sauri Hajia ta kalleshi wato ita zai rainawa wayo, Ammar na jin haka ya juya cikin takon k'arfi ya fice daga falon, cikin sanyin jiki Ummi tace "Umma sai mun dawo, Abba mun tafi." Amma sai dalla mata harara da tayi Alhaji kad'ai ya amsa da "A dawo lafiya Sa'ada." Wucewa tayi tasa gyalenta tana share yar k'wallar data tarar mata a ido, Amar ma bayanta ya bi ya dafa kafad'ar ta yana rarrashin uwatai, sai Junaid da shima ya musu sallama ya wuce, Jibril ma cewa yayi ya tafi sai Alhaji ne yace "To *B A* (sunan projet da yake aiki kenan, kasancewarshi d'aya daga cikin jigajigen ma'aikatar duk da k'arancin shekarunshi yasa Alhaji dama wasu daga mutanen gari ke kiranshi da haka) yau kuma wani garin zaku kaiwa girgiza?" Dariya yayi yace "Alhajin Allah kenan, yau tafiyar ba mai nisa bace, wani k'auye ne nan kusa nake so na shiga da kaina tare da sabbin ma'aikatan da muka d'auka, kasan sai ana nuna musu yanda aikin yake kafin su zama yan gari, amma komai dare zan dawo insha Allahu." "To Allah ya bada sa'a, Allah ya tsare." Cewar Alhaji, da murmushi ya amsa da "Ameen." Hajia ya kalla yace "Hajia ni na tafi saina dawo." Dayake shi ba daga tsatsonta yake ba sai kawai ta d'auke kai kamar bata ganshi ba, shi kuma ko a jikinshi dan in da sabo ya saba, wajen kakarshi ya nufa Husseina yace "Yar tsohuwa na tafi saina dawo." Da murmushi ta amsa da "A dawo lafiya d'an tsoho, Allah ya kiyaye." Umaima kyakyawar budurwa yar boko mai wayewa wacce ke koyon aiki (stage) a bankin da Amar ke aiki wanda shi dama *DG* (directeur général) ne a ma'aikatar, kasancewar gidan duk boko ne yasa ta samu hanya cikin sauk'i a ma'aikatar dan da kanta ta zab'i inda take so, kuma dama mata su kam Hajia tana basu damar yin abinda suke so, maza dai ne take son suyi wanda take so saboda tana son cimma wani burinta a game da hakan, ita ke biwa Junaid sai Jamila dake bi mata, duk da shekarunta har yanzu babu maganar aure a tsarinta, kuma dayake shi aure lokaci ne sai Hajia bata damu da lamarinta ba bare tace zata had'a ta da wani ko a cikin mazan gidan, doguwar rigar ce jikinta data kamata kuma ta fito da jikinta sosai, sai gyalen data d'ora da jaka a hannu kalar takalminta, ita ma gaishesu tayi ta kalli Amar dake rarrashin Ummi tace "Yah Amar ka jira ni mu tafi tare, mota ta na wajen gyara har yanzu." Juyowa yayi da kai ya mata alamar ta taho, da irin haka gidan yayi shiru ya rage sai iyayen, yara dama ana had'a musu abin kari ne su tafi dashi, in kaga sun zauna cin abincin kari to su suka zab'i abinda za'a dafa musu da safe, manya kuma dama babu wanda ya damu da abincin gidan, ba wai na safe ba har na dare ba wani sai yayi sati bai jefa abincin gidan cikin bakinshi ba, kuma hakan baya rasa nasaba da yawon gidan da kuma kowa na da 'yan canji a aljihunshi. Yanzu haka masu aiki ne su biyu gogaggu a fannin girki da kuma kula da tsabta wanda Hajia ta yarda dasu rik'a girka mata abinda zata ci ke ta kai kawo a madafa, d'aya budurwa ce sai babbar wacce bazawara ce, kafin ma ta yarda su fara aikin saida sukayi aiki a gidan na sati guda ta gamsu da abincinsu da kuma tsabtarsu kad'ai, sai guda biyu suma d'aya budurwa yar shekara *goma sha tara* da kuma dattijuwa su kuma aikinsu shara da goge goge, yanzu haka ma sune ke goge wajen cin abincin, sai Soueba da Zeinabou da su basu aiki ke jera kwanukan abincin, duk da ba su ke girkin ba amma suna taimakawa masu aikin, wani lokaci kuma suna girkawa da kansu, abin karyawa ana dafawa ne kawai, amma na rana dana dare sai wanda Hajia tace tana so, saida suka gama shiryawa Soueba ta zo cikin fargaba tace "Hajia an gama shirya wajen cin abincin." Wani kallo ta mata kamar kashi kafin tace "Ina zuwa to." Dukansu ne suka mik'e suka nufi wajen cin abincin, sai *Alhaji Labaran* mahaifin Jibril dayake shi d'an kasuwa ne yasa bai da k'ayadadden lokacin fita, gyara rigarshi yayi ya kalli Alhaji yace "Ni zan fita Alhaji, sai mun dawo kuma." "To Allah ya tsare, Allah ya bada abinda aka je nema." Amsawa yayi da "Ameen." Kallon Hajia yayi wacce tuni ta isa kan teburin Zeinabou da Soueba sun sakata tsaka suna zuba mata abinda ta zab'a, mahaifiyarshi ya juya yawa sallama haka ma Gambo da yake kallon agogon hannunshi saboda gudun wucewar lokaci, Soueba na ganin zai fita tayi saurin aje kwanon miyar zata nufi wajenshi, cikin akasi miyar ta d'an fallatso ga hannun Hajia, sai kuwa ta daka mata wata tsawa "Ke!" Cikin tsoro ta tsaya tare da kallon Hajiar, d'orawa tayi da "Ke mahaukaciyar ina ce? Me kike kallo da zaki k'ona ni da miya? Ko jarabar ce ta motsa ta miji? Ina ce ai fita ne zaiyi ko, meye kuma na hanzarin biyarshi a baya?" Cikin rawar murya tace "Yi hakuri Mama, ban..." "Ba kiyi me ba? Dallah b'ace min da gani." Labaran da yake jin duk abinda ke faruwa ko juyowa baiyi ba harya fita, Soueba kuma hanyar madafar ta nufa cikin sanyin jiki, tana daf da shiga taji tace "Ki turo min *Zeituna*." Juyowa tayi da ladabi tace "To Mama." Saida ta shige Alhaji ya kalleta kamar ya kifeta da mari, baya jin dad'in abinda take a gidan, yana son taka mata birki in tana irin wannan ikon nata, amma idan ya kalli yanda gidan suke girmamata da ganin darajarta mutumcinta ne zai zube yau da gobe idan yace duk sanda tayi ba daidai ba saiya tsawatar mata gaban mutane, dan wata rana iya shegen nata har gaban yara yi take, shiyasa yake bari sai sun keb'e wani lokacin yake mata magana, Husseina dai kallonta kawai take sai Gambo da shi dai yake fatan ma lokacin tafiyarshi ya kusa yayi abinda ya kawoshi ya bar garin kafin ta bijiro da wani abinda take so tace kuma dole yayi, suna haka Zeituna ta fito ta nufo wajen Hajiar, kallo d'aya zakawa budurwar kasan kyakyawa ce wacce Allah ya hore ma albarkatun jiki, amma talauci da rashin gyara yasa datti ya samu gurin zama a jikinta, tana kusa da k'arasowa Hajia ta d'aga mata hannu da fad'in "Dakata malama, koma kawai ma na fasa aiken na ki, jiki duk datti haka." Juyawa Zeituna tayi zata koma taji tace "Wai ke yaushe rabonki da wanka ma?" Pik'i-pik'i Zeituna tayi da ido tana kallonta hakan yasa tace "Anya ma kina wankan? Mtsss! Shiga ciki." Shiga tayi baiwar Allah sai kawai ta fashe da kuka, sai abokiyar aikin nata wacce ita dattijuwa ce da suke kira da *Iya* ta bata hak'uri tace ya kamata ace ta saba da irin haka, Zeituna kuma ciwonta d'aya shine wata jarabawa da Allah ya jarabeta da ita, babar jarabawa ce gareta kam, dan ace ubangiji ya jarabeka da son wanda bai ma son kanayi ba babbar jarabawa ce, gashi ita ba kowa ba kuma ba 'yar kowa ba, sannan matar da zata iya sakata ta shigo gidan ta tsaneta, ita kam dole tayi kuka, gashi tun bata san meye so ba take jin mutumin na birgeta duk wani motsinshi, har ta girma ta fahimci ta kamu da son mutumin da a haife ya haifeta, halayyarshi daban take ko cikin su uku d'in, duk da shine babban amma yafi sauran raha da barkwanci, tun tana tunanin birgeta ne yake har ta yarda *so* ne kawai, *son* wanda ba ma iya kallonta idonta bare ya fahimci ciwonta, *son* wanda yake da mata goggiyar 'yar boko, *son* mutumin daya sha boko ya k'oshi kuma yake da ilimi har na addini ma, *son* mutumin da ko zaratan 'ya'yanshi sun fi k'arfin ta bare kuma shi da kanshi, Iya nata rarrashi ita kuma tana wani tunanin daban, d'aga kanta tayi sama tana zubar da wasu hawayen ta furta a zuciyarta "Allah kai ka jarabeni da wannan ciwon, Allah ka kawo min maganinshi idan har ba ciwon da zaiyi ajalina bane, idan kuma wannan jarabawar ita ce silar ajalina, to Allah na rok'e ka ko sau d'aya ne ka had'a ido na dana *Abbansu Amar* ya fahimci son da nake masa, idan haka ta faru burina ya cika, ko a lokacin wa'adi na ya cika banda takaici ban kuma mutu da buri ba." Ba dan kar tayi sab'o ba da sai tace meyasa aka jarabceta da wannan k'addara, dan a ganinta bata cancanceta ba ko kad'an, amma kuma idan ta tuna da al'amarin ubangiji, yana da iko da k'arfin da zai juya daidai izuwa ba daidai ba, ya kuma juya ba daidai ba izuwa daidai, dan haka sai tayi shiru tana tunanin ko da Allah yasa soyayyarta batayi nasara ba, to tabbas ta koyi abu guda a wannan karatun, abun kuwa shine ta san ya *so* yake, ta kuma san zafin da ake ji da rad'ad'i lokacin da ka rasa wanda kake so, da wannan ta share hawayenta suka ci gaba da aiyukansu. *So* _(Mugun dafi)_ Zeinabou na tsaye ta rasa yanda zatayi, duk da suna zaunawa su ci abinci tare da su amma a takure suke, dan duk wanda ta kalla sai kiga tana yamutsa fuska kamar tana kallon amai, abunda ya faru kuma yanzu yasa ta rasa me zatayi, tana cikin wutsil wutsil da ido Hajia tace "Malama lafiyar tsaya mana a kai? Ki zauna mana." Da sauri ta koma kusan Husseina ta ja kujera ta zauna, ita bata ma buk'atar cin abincin amma dan kar tayi wani laifin yasa ta zauna, Gambo na ganin k'arfe tara da arba'in da biyar ya kallesu yace "Ina ganin ni zan tafi, dan nan da minti sha-biyar za'a fara taron." Cike da dattako Alhaji yace "To ba damuwa, Allah ya taimaka, Allah ya maku jagora a cikin al'amuranku, Allah ya kiyaye ya kau da idon mak'iya a kanku." Shima cike da jin dad'i ya amsa da "Ameen ya Allah Abba, mun gode Allah ya saka da alkairi, Allah ya k'ara lafiya da girma." Husseina ma addu'ar tabi shi da ita har ya mik'e tsaye, har lokacin kuma Hajia Zeeya ko kallonshi ba tayi ba, saida ya sunkuya yace "Hajia ni zan wuce, sai kuma na sake dawowa, idan da wani abu da kuke buk'ata sai ku fad'a min." A hankali ta kalleshi tare da nuna mishi wayar dake gefe akan teburin cin abincin tace "Wayar nan ta min tsufa, ina buk'atar sabuwa, kayan d'akina ma na buk'atar a canza su." Burinshi d'aya shi dai ya samu ya kubce ya tafi karta d'ora mishi abinda ba zai iya ba, dan haka jiki na rawa yace "Hajia wannan ai ba matsala bane, yanzu za'a canza komai kamar yanda kuke buk'ata." Alhaji ya kalla yace "Abba ku fa ko da wani abunda kuke so?" Murmushi yayi yace "Babu komai Harouna, Allah yayi albarka, Allah yasa ku gama da duniya lafiya." "Ameen Abba." Ya fad'a yana kallon Husseina yace "Hajia ku fa ko da abunda kuke so?" Ita ma kai ta girgiza tace "Ba komai wallahi Gambo, Allah ya tsare mana ku." Da ameen ya sake amsawa, da haka ya musu sallama ya fito, yana fitowa farfajiyar gidan ya samu masu tsaron lafiyarsa su biyu sai kuma dreba, mota uku ce saita tsakiya wacce yake ciki, dreban dake d'an garin ne ya had'a da neman sak'on Hajia, cikin masu tsaronshi kuma ya tuk'a motar suka nufi wurin taron. Abunka ga idan kud'i sun kwanta a wuri, sai gashi kayan d'aki da babbar waya sun hallara a gidan ahalin Gaga cikin awa d'aya zuwa biyu, kaya ne na gani na fad'a a ledarsu, aifa nan da nan da dreban da mai gadi tare da su Zeituna da Iya da sauran ma'aikatan aka fito da waccen kayan aka zuba sabbi, Hajia na zaune tana danna sabuwar wayarta, *takaici na d'aya ba'a fad'a min me take yawon dannawa a waya ba*, su Zeinabu da suka tsaya kan gyaran ne suka fito suka tambayeta yanda za ayi da tsofaffin kayan, cikin jiji da kai da isa da tak'ama Hajia tace "Ku har yanzu baku fahimci matsayina bane? Na gama da wannan kayan kuma, su ma waccen idan na shiga naga basu min ba zan kira shi ne kuma a sake min su." Husseina dake zaune ita ma a falon ce tace "Ai ba wani abu ba suka ce Hajia Zeeya, suna tambayar yanda za ayi da su ne, idan kika ce su zuba shara sufa cika aikinki ne kawai na su." Juyowa tayi kamar mai ciwon wuya ta kalleta tace "Na d'auka da su nake magana ko? Meye naki na saka min baki kuma? A gidana nake dole nayi iko da komai dake cikin gidan." Tab'e baki kawai Husseina tayi ta kawar da kanta, kallonsu tayi tace "Kuje duk yanda kuka yi wannan matsalarku ce, idan akwai mai buk'ata ma a cikinku zata iya sakawa a nata d'akin." Haka suka wuce da tunanin yanda zasuyi dasu, sai dai sun ci alhwashin ba zasu tab'a d'aukar ko da tsinke ne su bawa ko da wani na kusa da su bare su saka a d'akin su, dan wata rana saita goranta musu, dan haka a cikin d'akunan yara aka zuba wasu, wanda basu samu wuri ba kuma aka kai su ma'ajiyar kaya. *Wasu awanni baya* Ammar na shiga mota ya tayar ya tsaya bakin k'ofa yana jiran mai gadi ya bud'e masa, Amar ne ya fito tare da Ummi sai Umaima a bayansu, wani matashi ne cikin kayan soja ya matso kusan Umaimai, makulli ta bashi tace "Zan tafi tare da yah Amar, kai kaje ka dubo motar idan an gama gyaran saika d'auko." Tana fad'a ta wuce shi kuma ya bi bayanta ya fita, aikinsa kenan dama tuk'a iyalin colonel Hussein, Ummi na ganin motar Ammar tayi saurin k'arasawa ta bud'e ta zauna, da wutsiyar ido kawai ya kalleta dan yasan ta shigo ne dan ta fad'i abinda ke ranta, mai gadi na gama bud'e masa ya danna hancin motar waje ya harbata zuwa titi, ana d'aukar hanya Ummi ta kalleshi tace "Ammar hankalinka ya kwanta yanzu da aka ci mutumci na? Ka ji dad'i yanzu? To ka zuba ruwa k'asa ka sha dan farin ciki." Shiru yayi kamar ba dashi take ba, hakan yasa ta ci gaba da cewa "Ammar ku uku na haifa a duniyar nan, amma hatta k'aramin k'aninku da kuka bashi shekaru sha takwas ya fika sanin takamata, Ammar so kake sai bak'in cikinka ya kashe ni sannan ka huta? Gaba d'aya a cikin iyali ka zama wani baud'add'e ba'a gane gabanka, burinka kullum kasa Hajia ta min rashin mutumci akan laifin da ka aikata." Jingina tayi akan kujera ta ci gaba da cewa "Ka ci gaba dayi, kaga ranar daka tunzurata tasa mahaifinka ya sakeni sai kasa ya auro maka wata uwar, ko kuma idan na had'iye zuciya na mutu shikenan ai saiku huta." Kallonta yayi lokaci d'aya kuma ya d'auke kan shi ya mayar kan tuk'i, kallonshi ita ma tayi cikin jin zafi saboda yayi kamar ba dashi take ba, haushi ne yasa ta kai hannu da nufin kashe shi da mari ta bayan hannu, shi kuma dama yana kallonta ta wutsiyar ido dan haka yayi saurin gocewa, kallonta yayi yace "Ummi wai meye haka dan Allah, matar nan ya kamata ace ta daina damunku fa, haba." Da mamaki ta kalleshi tace "Ba zaka canza ba Ammar, idan kuma har akwai ranar bansan ko zan ganta ba." Ba tare daya kalleta ba yace "Duk da kun barni na tafi aikin da raina yake so da ku da ganina ma sai kun fara addu'a, idan kuma na mutu wajen daga to fa kune zakuyi kukan mutuwa ta." Da haka suka isa asibiti, suna zuwa Ummi ce baya shi kuma gaba, takaici ne ya rufeta ganin daga ma'aikata masu gadi da shara har zuwa malaman asibitin babu wanda ya kalla bare ya mishi magana, girgiza kai tayi a ranta tana fad'in "Da ace ba kama da mahaifinka kake ba, to ko ni kaina dana fara kokonto anya ni na haifeka." Faran faran ta gaisa da kowa ita ma ta shiga ciki, yau ma dai kamar kullum majinyata ya fara dubawa, duk wanda ke buk'atar wani agaji na gaggawa kuma saiya rubuta abinda yake buk'ata a kaiwa secrétaire ita kuma ta had'a ka da likitan da zai duba ka, daga cikin wanda Ammar ke bayar da umarni su duba majinyatan har da mahaifiyarshi wacce a gida ita ke iko, a asibiti kuma dole sai abinda yace domin kuwa shi docteur ne ita kuma infirmière ce, dan Ammar saida ya kwashe shekara sha hud'u a *France* yana karantar *Cardiologue* kafin ya zama cikakken likitan zuciya, duk da Sa'ada ita ta so zama *doctorat* amma daya zama sai ta tsallake k'asarta taje wata k'asar yin karatu na shekara takwas sai kawai Hajia tace sam ba da ita ba, idan kuma suka ce zasuyi to ba da yawunta ba, dole ta hak'ura sai shi Ammar ya tafi, da wannan diplôme d'in ne suka samu damar bud'a asibiti ta su ta kansu. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Misalin *10:00* gwamna Gambo ya sauka babban birnin niamey, nan ma motoci ne suka iso d'aukar shi harda motar sojawa dan tsaron lafiyarsa, tun a hanya ya kira Amar ya fad'a mishi a cire kud'i a counte d'in shi ya bawa su Hamna saboda kusan wata uku bai musu aike ba, kuma gashi yanzu suna ecole ya taho, Amar da a lokacin ke tsaye gaban teburin Umaima yana d'an nuna mata wani abu daya shige mata duhu ya amsa da to, ba b'ata lokaci Hamna da Amna dake cikin aji sak'o ya shigo wayoyinsu na an turo musu da kud'i zasu iya zuwa su cira, farin ciki wurin Hamna ba magana dan dama bikin k'awar ta ake daf da farawa nan da kwana uku, har yanzu ko anko bata siya ba kuma bata damu ba dan tasan zata siya. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Misalin *12:20* dreba ya d'auko yara da daga ecole, zuwansu yayi daidai da zuwan Ammar dan sha biyu yake saukowa, wani lokaci kuma ya kan koma k'arfe hud'u ya ga wasu, wani likaci kuma sai takwas na dare, yana fitowa daga mota yaran suka dinga gaishe shi, da ido ya bi kowane yana kallo har suka shige ciki, juyawa yayi yana kalkad'a makullinshi ya nufi na su b'angaren. *12:50* motoci uku suka tsaya k'ofar gidan, biyu daga cikin motocin na sojoji ne sai wacce ke tsakiya ita ce babba k'irar *Prado*, da sauri sojan dake tuk'a motar ya fito tare da zuro hannu ya bud'e mazaunin baya, colonel Hussein ne ya fito da k'arfin shi, yana fitowa sojojin suka k'ame suna sara mishi, saida ya kallesu ya sara musu sai suka saki na su hannu shi kuma ya wuce ciki tare da rakiyar soji biyu, saida ya kai k'ofar shiga falo suka tsaya shi kuma ya juyo ya kallesu yace "Dukanku zaku iya tafiya, amma *sajan* (sergent) Idris zai iya tsayawa." Yana fad'a ya wuce suka bishi da "Ok chef." Duk wanda ya shiga wanka yake farawa da shi, ga mai buk'ata kuma ya nemi abinci ya ci sannan ya kwanta ya huta, amma colonel bayan sun dawo daga masallacin juma'a tare da Ammar bayan gidan suka nufa inda ke da fili da tarin shukoki da kuma kayan motsa jiki barkatai suka fara abinda suka saba indai suna tare, haka ya zage ya dinga koya mishi horon soja wai saboda kare kai kuma tunda yana son abun, a k'alla sun d'auki awa d'aya kafin suka had'a gumi kowa ya shiga dan yin wani wankan, bayan colonel ya shiga yayi wanka ya fito ya canza kaya, zai fita Hajia Zeinabu tace "Yallab'ai ina son magana da kai fa." Dawowa yayi ya zauna bakin gadon yana kallonta yace "Uhum." Duk da bata had'a ido da shi ba amma gabanta fad'uwa yake, haka ta daure tace "Dama ina so na ji ko yaushe ne hutunka zai k'are?" Fuskar nan ba fara'a yace "Tun yaushe nake garin nan? Ba kya lissafi ne?" Cikin rarraba ido tace "Ba haka bane, dan naga yanayin aikin naku ana iya kiranku ma ko wa'adin bai cika ba." Tsura mata ido yayi yace "Me kike so ki fad'a?" "Kawai zaman gidan nan ne ya gundure ni, ina buk'atar wani abu da zai rik'a deb'e min kewa, tunda na ga ita Sa'ada tana zuwa aiki, kuma ba finmu tayi ba karatu ne kawai bamuyi ba." Wani kallo ya sake mata kamar zai had'e ta kafin ya mik'e yace "Alhamdulillah da Allah yasa da mai hankali nake magana ba mahaukaciya, ashe kinsan sai wanda yayi karatu ne zai iya shiryawa yace zai tafi wajen aiki?" A tak'aice tace "Kai ma ci mana mutumci zakayi?" "Kinga Zeinabu, matsalata dake tsegumi, kuma rashin wayewarki ne ya haddasa miki haka, shiyasa na so tun farko ki shiga ko da makarantar yak'ida jahilci ce amma ki ka k'i, ga Jibril nan kina ganin aikinsu kenan kullum, idan kinso ko shi zai iya yi miki hanyar samun hasken k'wak'walwa." Kallonshi tayi da takaicin abinda yake fad'a mata tace "Dan bana da ilimi shiyasa dama ba ka iya zuwa ko ina dani, to ai sai ka d'auki karuwan naka ka dinga yawo da su tunda sun fini." D'an cije leb'en shi yayi yana kallonta yace "Ni kike fad'awa ina da karuwai Zeinabu?" A yanda yake kallonta tasan tsaf zai mareta dan ba bak'on abu bane a wurinsu, duk da baka shaidar mutum amma a zahirance zata iya cewa mijinta baya shan giya ko neman mata duk da kasancewarshi soji, dan duk inda yake ya ji shaid'an na neman kaishi ga aikata zina haka zai biyo jirgi ya zo wajenta, dan har doguwar tafiya ya tab'a yi ya zo kuma ko awa baiyi ba ya koma, matsalarshi d'aya saurin hushi da marin fuska ko harbi da k'afa idan ta mishi nisa, shi ma kuma ya fad'a mata ta dinga kiyayewa tana sanin me zata fad'a mishi saboda yana da zuciya tun fil'azal daman ba wai dan yana soja ba, amma inda aka samu matsalar Zeinabu irin matan nan ne masu tsegumi da ganin an musu ba daidai ba, dama dama Hajia na gyara musu zama, amma in zaiyi shekara baya gari ya samu hutun wata uku ya zo sai tace ga abinda akayi, kuma idan ka duba sai kaga k'orafi ne kawai na banza da wofi, gashi matsayin wasu yana tsone mata ido musamman Sa'ada, ta mayar da ita kamar kishiyarta duk wani motsinta akan idonta, sanin halinshi yasa ta kawar da kai gefe tana gunguni tana fad'in "To k'arya na fad'a? Matan ne baka kul...?" Bata gama fad'a ba taji saukar yatsu biyar a fuskarta, d'ago fuskarta yayi cikin d'aga murya yace "Kalleni nan ki fad'i duk abinda ke ranki, ke har ni zaki mayar d'an iska, dan kinga na zauna tare da ku har na wata biyu shine zaki d'auke ni wani mahaukaci, to yau zan bar miki garin sai ki d'auki tsiyar da kike d'auka idan bana nan, aikin banza." Ya fad'a yana barin d'akin, tana ganin fitarshi ta d'ago tace "To ka tafin mana sai me? Idan baka nan b'acin raina yana raguwa ne da kaso arba'in cikin d'ari, kai ka k'unsa min bak'in ciki mahaifiyarka ta tusa min, mun zama kamar bayi a gida duk saboda bamuyi karatu ba." Ko da su Hamna suka dawo aka fad'a musu Abbansu ya tafi basuyi mamaki ba, dan haka basu damu ba saima shirya fita da sukayi da yamma dan su siyo ankonsu suma, baccin rana sukayi ko da suka tashi la'asar tayi sai suka shirya cikin dogayen riguna bak'ak'e iri d'aya, komai na jikinsu kala d'aya suka saka ta yanda ba zaka iya tantacewa cikin sauri ina Hamna ba ko Amna, tun a d'aki suka fara rigima moton wa za'a hau? Nan Hamna tace ai da nata aka tafi école, Amna kuma tace jiya da nata ai aka tafi, k'arshe dai dana Amna aka tafi dan dukansu basu damu da matsayinsu ba ko na mahaifinsu, shiyasa ko dreba basu damu a d'aukar musu ba bare a siya musu mota. Tun a falo suke jiyo hayaniya a farfajiyar gidan, can suka samu yara da iyayen ana ta hira sai dai babu Hajia babba, saida suka dawo d'akin ta da sallama amma ba'a amsa ba, wata sallamar suka sake yi Hajia dake zaune tace "Ku shigo mana." Shiga sukayi duk jikinsu yayi sanyi dan kar ta hana su fitar, Hamna ce tace "Hajia barka da yamma." Kallonsu kawai tayi bata amsa ba dan haka Hamna tace "Hajia dama..." "Dama me?" Ta katseta, d'orawa tayi da "Fita zakuyi ko? To ku tashi ku tafi, amma ke Hamna ki sani na barki ne saboda na ganku tare da Amna, dan na lura duk shegen bak'in halin uwarki ne kika d'auko na rashin son zama wuri d'aya." Shiru sukayi har saida tace "Ni ku tashi ku bani wuri, saura kuma idan kun tafi karku dawo sai an aika nemanku." Mik'ewa sukayi sai Amna da tace "Mun gode Hajia, insha Allahu ma ba zamu jima ba zamu dawo." Suna fitowa Hamna ta yaye kallabinta ta zubo da manyan kitsonta na gashin doki har gadon baya tare da fad'in "Shikenan dan uwarmu bata gidan saiki d'auki karan tsana ki d'ora mana, dad'in ta dai bamu muka kashe musu auren ba." Suna fitowa farfajiyar suka kalli matan suka ce "Su tanti (aunty) sai mun dawo." Hamna ce ta tuk'a mai gadi ya bud'e musu k'ofa suka fita, a k'ofar gidan suka samu colonel da Ammar zaune kan kujeru, hira ce suke amma babu mai annuri a fuskarshi, dama kana ganin Ammar na hira ne da mutum biyu a duk fad'in gidan, ko dai colonel ko kuma Gambo, da kaga dariya ko murmushinshi to Gambo ne, tsayawa tayi tace "Kawu ana hutawa?" "Ina zakuje kuma da yammar nan?" Ya jefo musu tambayar, cikin turo baki tace "Kawu zamu je yar kasuwa ne, amma yanzu zamu dawo." Kunna moton tayi yace "To dan Allah ku kula da kyau, sannan karku yarda magriba ta muku a waje." "To kawu." Ta fad'a tana murd'a moton, kallon Ammar tayi tace "Boss ba ko magana." Sai lokacin ya d'ago idonshi ya sauke a kanta amma tuni harta ja moton da k'arfi tana mishi dariya, dariya colonel yayi yace "Saika nuna mata kai boss d'in ne ko zaku kwashe lafiya da ita." K'ala bai ce ba shi dai dan yana so ne ya lissafa duk iskancin data masa ta yanda idan ya damk'eta zata gane shayi ruwa ne, inda shi kuma colonel yake mamakin yanda Gambo ya bar yaranshi sakaka a gari haka ba zaka tab'a cewa wasu 'ya'yan manya bane, sa'a d'aya ma yaran su kansu basu damu ba harkar gabansu suke. Tashi colonel yayi ya shiga cikin gida yana jin shi sakayau, dan dama sai mutum ya zo hutu ne yake samun 'yanci da sakewa, ya shiga ne da niyyar yin wanka ya kuma had'a kayanshi, dan yayi niyya saiya bar garin ko zeinabu ta ji dad'i, ya shiga d'aki kenan ya aje wayar zai shiga ban d'aki sai wayar ta fara ruri, dawowa yayi yana kallon mai kiran, d'an uwanshi ne wanda yake da tabbacin yana garin nan wato Abban su Amar, to meyasa yake kiranshi? Tabbas ba lafiya zuciyarshi ta gaya mishi, d'auka yayi ya d'ora a kunne, daga b'angaren lieutenant yace "... *Me kuka ya faru ko zai faru?, sai mun had'e a shafi na gaba insha Allah.* 18/05/2020 à 13:51 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 _Bismillahir rahamanir rahim_ _4_ Lieutenant ne yace "D'an uwa kaga na kiraka ko? Dama yanzu na samu wayar *Aisata* (babbar d'iyar Fatime kanwar Hajia) take fad'a min Allah yayi wa Hajia (mahaifiyarsu) rasuwa." Takawa colonel yayi gaba yana fad'in "Subhanallah, Hajia kuma? Yaushe? Dama bata da lafiya ne?" Wani d'an murmushi lieutenant yayi yace "Haba d'an uwa, mutuwa ai ba sai ba'a lafiya ba take zuwa, dan nima dana tambaya Aisata ta fad'a min yau da safe ma har unguwa Hajiar ta fita, kawai dai lokaci ne yayi." "Ikon Allah, kaga wata mutuwa bagatatan, yanzu to ya zamu sanar ma da Hajia?" "Shiyasa na kiraka d'an uwa, dan kaine soja watak'ila ka fini sanin dubarun kwantar da hankali." Yanda ya k'arashe maganar cikin zolaya yasa colonel cewa "Ba fa nasan iskanci, ka d'auka a sojan rarrashin mata da soyayya ake koya mana ne, ai wannan aikin ko Ammar ba zan sa shi ya fad'a mata ba." Dariya lieutenant yayi ya mik'e daga kan teburinshi wanda ke cike da tarin takardu da tarkace yace "To ni dai na fad'a maka kasan yanda zakayi karka d'aga mana hankalin uwa, yanzu haka gani nan tafe zuwa gidan zan canza kaya, dan ina so na samu bisar Hajia dan sunce k'arfe hudu da rabi za'a rufe ta." Da sauri colonel ya kalli agogon dake d'akin yace "Eh to, kuma kaga fa da sauran minti talatin da wani abu, kana ganin zamu iya isa *Gidan roumji* nan da wannan lokacin?" "Sosai ma, kai dai kawai kuyi harama, duk wanda yasan zaije ya kimtsa da wuri mu d'auki hanya, zan kira Labaran na fad'a mishi shi ma nasan zaije." "Shikenan." Yana fad'a ya kashe wayar ya shiga neman wata lambar, ana d'auka ya bayar da umarnin motocin d'azu su dawo zai fita shi da iyalinshi, yana gamawa ya shiga wanka cikin k'ank'anin lokaci ya fito ya shirya cikin bla (bleue) d'in shadda amma kanshi ba hula, wayarshi ya figa ya fito ya nufi d'akin Alhaji, ba wani b'ata lokaci ya fad'a mishi abinda ke faruwa tare da cewa su fito yanzu zasu d'auki hanya, lieutenant ma na shigowa wanka ya zarce kai tsaye ya shirya da gaggawa, Alhaji da kanshi ne ya samu Hajia a d'aki yace ta saka gyalenta zasu fita, tayi tambayar ina? Amma bai bata amsa ba, da haka ta fara gunguni tana saka tsadadden gyalenta ta d'auki takalmi masu shegen kyau da jakarsu ta saka, waya a d'aya hannu sai mouchoir (handkiciep) a hannu na goge k'ura da datti, haka ta fito cikin takon izza da k'asaita suka nufi k'ofa, a farfajiyar gidan suka samu mata da yara, lieutenant ne ya kalli matan yace "Mu zafi tafi gidan roumji sai Allah ya mana dawowa, akwai yiwuwar mu kwana acan, dan haka ku kula da gidan da yaran." Zeinabu ce ta kalli mijinta tace "Wani abun ne ya faru yallab'ai?" D'an juyawa yayi ya kalli Hajia da sai wani yamutsar fuska take ya kuma kalleta yace "Ba komai, zamu kiraku idan mun isa can, kuma gobe zan turo a d'auke ku." Muryar Hajia ce ta katse shi tace "Wai meye ya faru a gidan roumjin? Ko dai wani abu ya samu Fatime ne?" Lieutenant ne yace "Ba komai Hajia, idan munje sai muji meke faruwa." Cikin had'e fuska tace "Ku tabbatar ba wahalar banza zaku sani nayi ba, dan na tsani na kwashi jiki na je k'azamin wuri kuma ba da wani dalili ba." Kafin wani yace wani abu Labaran ya shigo a hargitse da sallama, kamar wanda yayi gudu yace "Wai har kun shirya? To zamu iya tafiya kenan?" Cikin tafiya kamar ta saurayin doki Ammar ya shigo saboda kawu Labaran ya fad'a mishi komai, lieutenant ne ya kalli Ammar fuska ba walwala yace "Ka kira sauran yan uwanka ku same mu acan, ba wai kowa yayi tafiyarshi ba nake nufi, ku tabbatar kanku a had'e kuka tafi, kai kuma ka wuce ka canza wannan kayan na jikinka, kar wanda ya kuskura ya zo mana da shigar turawa a wurin jama'a." Kamar wanda ciwon kai ya dameshi haka ya juya ya nufi b'angaren su ko magana babu, su kuma suna jin tsayawar motoci suka fito, colonel da kanshi ya bud'ewa su Alhaji suka shiga motarshi mazaunin baya, shi kuma wani soja ya bud'e mishi ya zauna gaba, motar soji ce gaba saita colonel sai kuma wata motar ta soji a baya, sai motar Labaran wacce lieutenant ke ciki suka d'auki hanya, tunda suka samu titi suka bud'e wuta ake gudu sosai saboda suna so su isa da wuri, a lokacin ne Alhaji ya kalli Hajia ya fara da bata hak'uri da kuma tausarta kan haka Allah ya so, nan ya fad'a mata k'anwar ta ce ta rasu, dafe k'irji tayi tace "Fatime, ta rasu?" Kallon titi tayi tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Fatime lokaci yayi, shikenan yer uwata ta tafi ta barni." Jimami ta dinga yi amma dai babu kuka ko alamun razana a tare da ita, da haka kuma cikin ikon Allah sai gasu gidan roumji cikin minti ashirin da bakwai, ko da suka iso anata shirya shiryen kawar da ita, nan Hajia ta shiga cikin ciki mazan kuma suka shigar da mitocisu cikin layin masu rakiyarta gidanta na gaskiya. Ko da Hajia ta shiga gidan bata gaisa da kowa dake waje ba tayi cikin d'aki cikin jagorar autar margayiya duk da kana ganinta zaka san tasha kuka, tana shiga d'akin ganin mutane ga zahi yasa ta wani had'e fuska tasa jelar gyalenta ta fara firfita, autar Fatimen ce tace "Hajia ku shigo nan ciki." Bayanta ta bi har suka shiga d'akin margayiya, kan gado ta zauna inda autar ta juyo mata da pankar dake aiki, juyawa tayi zata fita Hajia tace " *Sayyada*." Juyowa tayi ta amsa da "Na'am Hajia." Cikin gatsina fuska tace "Ki bud'e min tagar nan." Ta fad'a tana nuna mata tagar dake gefe da yatsa, da sauri ta bud'e mata sannan ta juya ta fita, kafin ta shigo kuma mutanen da suka shigo gaishe da Hajia da yi mata ta'aziya basu da adadi, duk da ita bata kula su ba amma dayake a dangin kaf babu wanda Allah ya hore ma abun duniya da matsayi da iko kamar ita, shiyasa suke girmamata suma a dolensu, har yaran margayiya su ne da kansu suka shigo akayi wa juna jaje, suma mazan suna dawowa daga bisa suka shigo aka k'ara jajantawa da bawa juna hak'uri, saida mutanen suka tsagaita Sayyada ta shigo da karap (jug) mai kyau da kofi ta zubawa Hajia gumbar da aka had'a mai sanyi, tana mik'a mata ta girgiza kai tace "Um um bana sha." Duk da ba gari d'aya suke ba amma Sayyada tasan ta farin sani, dan haka bata damu ba ta juya zata fita da shi sai kuma tace "Kinga, idan kin fita..." Sai kuma ta kalli wayarta tace "Jeki ma ya isa." Fita tayi inda ita kuma ta d'auki wayarta ta dannawa colonel waya dake zaune k'ofar gida, yana ganin lambar Hajia saida gabanshi ya fad'i saboda tunanin abinda za tace masa yayi, cikin sauri ya d'auka ya aza saman kunne tare da fad'in "Assalama alaikum Hajia." Cike da iko da nuna ita ce gaba dashi tace "Ruwa mai sanyi da lemun da kasan ina sha nake so, ba kuma wani nake buk'atar ka aika ba, kai da kanka zaka je ka samo sannan ka kawo min, ina d'akin Fatime." Tana gama fad'a ta datse kiran, d'auke wayar yayi a kunne ya kalli lieutenant dake kusanshi mutane na ta kallonsu abun birgewa saboda ganinsu iri d'aya sak, yunkurawa yayi zai tashi lieutenant yace "Ina zuwa kuma? Lafiya dai ko?" Cikin rad'a yace mishi "Zanje aiken Hajia, yanzu zan dawo." Kallonshi yayi da kyau yace "Amma ga yaranka nan ka basu mana." Had'e fuska ya sakeyi ya wuce bai kula shi ba, yaranshi dake gefe suna ganin haka suka matso suna sara mishi, ko kulasu baiyi ba ya saka takalmi zai fara tafiya ya ji suna take masa baya, juyowa yayi rai b'ace yace "Meye kuma na bi na, ku jira ni na dawo to, wannan ba aikin général bane ko aikin k'asa zanje yi, uwata ce ta aike ni, ko dole sai kunga me zanje yi." Yana fad'a ya wuce kamar zai tashi sama musamman abinka ga tafiyar mai k'arfi, su kam da bayar da hak'uri suka bi bayanshi suna jinjina girma girma ne, duk girmanka da tsiyarka uwa ko uba ko mata sai su juyaka, kai idan ma ka zama lusari har 'ya'yan daka haifa sai su juyaka yanda suke so, da k'yar ya isa shagon daya samu duk abinda take so, da kuma yasan cewa tana son yaour sosai sai kawai ya siyo ita ma, dan k'aramin aikinta ne saiya kawo tace kuma tana son ta, haka colonel ya kinkimo bak'ar ledarshi a hannu ya taho da ita, sabo da kuma sanin kan aiki yasa d'aya daga cikin yaranshi suna ganinshi yayi saurin mik'ewa zai nufi wajenshi, wasu jajayen idanu colonel ya zaro mishi hakan yasa ya k'ame wuri d'aya, cikin gidan ya haura ya shiga ya wuce d'akin, yana zuwa ya sameta zaune ita kad'ai a d'aki kamar mayya, ita ba zata iya shiga mutane ba saboda k'yank'yamin su take tana ganin ta wuce ajinsu, durk'usawa yayi akan tafukan k'afafun shi ya fara bud'e ledar yace "Hajia ruwan zan baku?" Ba tare data kalleshi ba tace "Umm." Bud'awa yayi ya bud'e murfin robar ya mik'a mata, karb'a tayi tasa abin goge gogen nan na hannunta ta goge bakin robar sannan tasha, gefe ya aje mata sauran yace "Ga sauran nan Hajia ko zaku buk'ata." Wani kallo ta masa tace "Hussein yanzu dayawa ka siyo saboda kar anjima nace ina so ka sake wahala? Tafiyar ce ka ke jin wahalarta ko me?" K'asa yayi da kanshi yace "Ba ko d'aya Hajia, na dai siyo ne ko zaku iya buk'atar su a kowane lokaci." Cikin b'acin rai tace "To bana so Hussein, ka d'auka ka fitar min da su yanzun nan, idan buk'atar ta tashi zan sake nemanka." D'aukar ledar yayi yace "Shikenan Hajia, Allah ya huci zuciyarki." Har ya kusa kaiwa k'ofa tace "Ka ban lemu d'aya." A hankali ya bud'a ledar ya fito da kwalin lemu ya sunkuya ya aje mata k'asa gefenta, yana d'agowa suka had'a ido ta mishi wani kallo tace "Cewa nayi fa ka bani, shine zaka aje k'asa." "Yi hak'uri." Ya fad'a yana sake d'auka ya bata ga hannun, amma sai cewa tayi "Aje kawai zan d'auka." Ajewa yayi ya juya ya fita yana addu'a a ranshi Allah ya k'ara musu hak'urin zama da mahaifiyarta su, dan iyaye irin mahaifiyarsu wuyar sha'ani ne da su ba kad'an ba. Lieutenant ne ya kira Gambo ya sanar da shi, nan fa aka bi duk 'ya'yan margayiya ana bashi yana musu ta'aziya, kafin daga bisani ya sake cewa a mik'a ta'aziyarshi ga kowa dake wuri dan ba lallai ya samu lokaci ya zo ba tunda ya riga da ya bar garin. *Bayan tafiyarsu* Ammar n ma shiga d'aki ya fara tunanin wanda ma zai fara kira a cikin su ukun, tunda Jibril shi baya garin watak'ila zuwa gobe yaje idan ya dawo, ba komai yake dubawa ba sai doguwar maganar da zaiyi da su, kuma ya tabbatar duk wanda ya kira saiya tambaye shi ya akayi? Ya ake ciki? Me ya faru, me zai faru? Dan haka ya yanke shawara ya kuma rubuta sak'o ya had'e duka lambobin nasu ya aika musu, kowa na inda yake wannan sak'o ya shigo na su zo gida yanzun nan zasu wuce gidan roumji Hajia Fatime ta rasu, duk basuyi mamakin ganin sak'on ba saboda ganin wanda ya turo shi, cike da jimami kowa ya antayo motarshi ya nufo gidan. Kamar had'in baki saiya zamana babu wata tazara tsakanin zuwan nasu, kuma kowa b'angaren su yake nufa dan ya shirya babu mai tunanin aiki gobe tunda dama asabar ce, sa'a akayi Junaid zai shiga d'akin shi Amar kuma ya shigo falon, nan Amar ke tambayarshi "To wai yanzu hanya zamu d'auka kenan?" Junaid ne yace "Yanzu ba wannan ba, mu fara saurin kimtsawa dai, daga nan sai mu san abinyi, dan kasan gidan nan akwai yan gaggawa dayawa, babu wanda zai jiramu idan..." Fitowar Ammar cikin bak'in yadi shara-shara har ana ganin farar rigarshi yasa sukayi shiru suka kalle shi, kamar dai kullum fuska a tamke ya kalli Junaid yace "Su waye yan gaggawa a gidan nan?" Juyawa Amar yayi ya nufi d'akin shi yana fad'in "Na gode Allah da yasa tambayar nan taka ce d'an uwa, fatan alkairi." Junaid kuma murmushi yayi yace "Ah haba dai soja, cewa nayi dayake gidan nan akwai..." Da gudu ya shige d'akin shi ya rufo k'ofar daga ciki yake fad'in "Yan gaggawa na ce, kuma kaine farko, sai wannan kawun naka (mahaifinshi kenan) colonel yake ko me ma." K'anan Jibril ne ya shigo da sauri wanda yake da tare da mahaifinshi Labaran a kasuwa suna kasuwanci shi ma ya shigo dan shine na uku da Ammar ya turawa sak'on duk da suna gaba dashi nesa ba kusa ba, kallonshi Ammar yayi yace "Ka fad'a ma yaran nan ina jiranku waje nan da minti biyar, idan lokacin nan ya cika baku fito ba, to zan tafiya ta ne tunda kowa da motarshi ai, amma ka fad'a musu umarnin Abba ne yace mu tafi tare." Yana gama fad'a ya fice daga d'akin inda *Jamil* ya bi dak'unan daya nuna mishi da kallo, k'wank'wasa musu k'ofar yayi ya sanar da sak'on Ammar kafin shima ya shiga dan shiryawa. *Minti hud'u* Amma ya fara doka wata uwar oda data firgita duk wanda ke cikin gidan, wad'anda suka san da su ake tuni suka gigice suka rasa ma abunyi, ba tare daya daina odar ba sai kuwa gasu da gudu suna rige rige, Jamil bawan Allah ko d'akin shi bai rufe ba ya taho da gudu da takalmi a hannu da k'yale alamar gogewa zaiyi ko yake cikin yi, bud'e k'ofofin motar sukayi suka zauna Junaid yace "Dan girman Allah odar ta isa haka, gamu nan fa mun shigo ko." Amar ne ya doka wani uban tsaki saboda sai lokacin ya kula da abin goge bakin (brush) daya taho dashi a aljihu, juyawa sukayi suka kalle shi ai sai Junaid ya kwashe da dariya, cikin jin haushi Amar dan ko turare bai fesa ba yace "Kai ban son k'ananan iskanci fa." Mayar da kallonshi yayi ga Ammar yace "Allah Ammar ba ka kyautawa, yanzu shirin ma ka barmu mu tafi a tsanake amma ba zaka iya ba, wane wace irin rayuwa ce, haba." Juyowa yayi ya kalleshi ya had'e girar sama da k'asa yace "Kar ka fad'a min maganar banza, yan daudu ne ku ko mata da zaku ce shirinku na buk'atar b'ata lokaci?" Cikin jin zafi Amar yace "Yan daudun ne kamar kai ba, ai kai gashi nan ka shirya a tsanake babu wanda ya takuraka, sai mu daka raina, wallahi ba dan ance Abba ne yace mu tafi tare ba da babu tsiyar da zata sanya na tafi da kai, tunda ai motarka ba fin tawa motar tayi ba." Idon Ammar ne sukayi launin ja ya fito daga motar da k'arfi tare da zagayowa inda Amar yake a baya yana fad'in "Amar ni kake kira d'an daudu? Ni? Ni sa'anka da zaka kirani da d'an d...?" Junaid ne yayi saurin rik'e Ammar d'in saboda bud'e murfin motar da yayi zai daki Amar da shima ke shirin fitowa, fitowa yayi a hassale shima yace "An kiraka d'an daudu, mu daka kamalta mu dasu bamu da zuciyar jin zafi ne ko me? Sai kai daka fi mu sanin ciwon kanka kenan, uban son girman tsiya, tsakani na da kai ko minti biyu babu, amma kullum kai ganinka ka girmeni da wata tazara mai tsayi." Junaid dake ta rik'on Ammar yana bashi hak'uri cikin b'acin rai ya sa gwiwar hannunshi ya buge shi a baki yana fad'in "Dallah sakeni malam, kana ji yaro yana fad'a min magana son ranshi." Junaid daya ji hanb'ara a baki baisan sanda ma ya sake shin ba, tuni jini ya gabce mishi harda hanci ma, sai kuwa Ammar ya cakumi wuyan Amar da hannu biyu ya shak'e shi sosai yana fad'in "Ni kake wa iskanci, ko sakan d'aya na baka ince dai ni na fara shan iskan duniyar? Shine zaka tsaya kana raina min wayo dan kawai kunga ina k'yale ku." 😔 'Yan biyu a madadin had'in kai sai gashi Ammar da Amar suna dakuwa kamar yara k'anana, amma Amar yafi galabaita saboda har yanzu Ammar bai sake shi ba daga shak'ewar daya mi shi, duk da haka kuma sai kai yake buga mishi a nashi kan, a d'aya b'angaren kuma yasa gwiwar k'afar shi sai tokara mishi yake a ciki, shi kuma duk dukan da yake ma Ammar d'in ma ba ji yake ba, ai kuwa gani Ammar zaiyi kisan kai yasa Junaid dake jinyar kanshi da Jamil suka fara k'ok'arin b'anb'are shi, dan tuni fuskar Amar ta fara had'a jini daga baki da hanci, amma saboda bak'ar zuciya ta Ammar sai ya dinga kai musu haura suma, ana cikin haka Ummy da ta ga mutuwar Hajia Fatime a kafar sada zumunta na alahlin Gaga ta taho gida suka ji muryar ta tace "Junaid, Jamil, ku barshi ya kashe shi." Tana fad'a ta wuce b'angaren su ko kallonsu batayi ba, su Junaid kuma basu bar raba su ba saida Junaid ya tattara k'arfin shi ya fizgo Ammar daga jikin Amar yana fad'in "Dallah malam sake shi ko." Amar na jin ya samu numfashi ya durk'ushe a wurin yana mayar da numfashin wahala, Jamil ne ya taimaka mishi ya mik'e suka nufi b'angaren iyayen sai Junaid daya bi bayansu bayan ya k'arewa Ammar kallo wanda ya buga murfin mota da k'arfi ya juya ya koma b'angaren su, suna shiga ciki suka ci karo da Zeinabu da faranti a hannu, tana ganin Amar a yamutse tace "Jamil lafiya? Meya same shi haka? Allah yasa dai ba hatsari yayi ba." Kafin ya bata amsa Junaid ya shigo bakinshi har ya fara kumbura kuma har yanzu yana fitar da jini kad'an kad'an, da sauri ta saki farantin ta k'arasa ga Junaid tana fad'in "Kai wai lafiya? Meya sameku ne haka?" Cike da k'aguwa Junaid ya d'an janye hannunta data tab'a shi yace "Umma ba komai, ba had'ari mukayi ba." A lokacin Jamil harya zaunar da Amar kan kujera ya nufi d'akin Ummy dan ta fito ta duba shi, Zeinabu ce ta kalli Junaid tace "In ba had'ari kukayi ba to me kukayi? Dubeku fa." Shima zama yayi a kujera ranshi a b'ace yana murza bakinshi, Soueba ba ta fito yayi daidai da fitowar Jamil dan Ummy tace babu inda zataje can su suka sani, Soueba ce ta kalli Jamil tace "Kai wai lafiya; meya faru ne haka? Meya samu Amar d'in." Cike da damuwa yace " Mama ba komai, dan Allah kije ki samu Ummy ki fad'a mata Amar na zubar da jini ta zo ta duba shi, ni na mata magana amma ta k'i fitowa." Amar na jin haka ya mik'e ya nufi d'akin Ummy duk da jirin dake son kwasar sa, cikin fad'a da hushi Zeinabu tace "Wai duk uban da aka tambaya sai yace ba komai bayan ga komai d'in, to koma menene ya faru ba sai ku fad'a ba, idan har kunsan ba zaku fad'a ba meye na shigo mana d'in? Wato inda iyayenku ne maza suka k'ura muku ido da tuni kun sakar musu zance, amma dake mune marainanku da muke wasa da ku kowane na hancin uwa sai dai yace ba komai, to kuje da ku da ba komai d'in duk kun ci uwarku." Cikin b'acin rai Junaid yace "Dan Allah Umma meye haka? Mun fad'a miki ba komai ba shikenan maganar ta wuce ba, zaunawa zamuyi mu fad'a muku Amar da Ammar ne suka samu sab'ani har ta kaisu ga doke doke." Mik'ewa yayi zai bar d'akin dan yana jin haushin surutun uwarshi da tseguminta, abun magana da ba na magana ba ita duk d'aya ne a gurinta, da gudu gudu ta tare gabanshi tana kallon bakinshi tace "Ammar fa ka ce? Halan kai kuma tsakaninsu ka shiga shiyasa ya maka wannan dukan?" Rab'ata kawai yayi ya bar d'akin hakan ya k'ara hassalata ta fara d'aga murya tana fad'in "Ni na sani mana wani abu ai sai wannan mugun, wai shi Ammar meya d'auki kanshi a cikin gidan nan ne? Haka kawai ka addabar mana yara basu da damar da zasu wataya a gidan ubansu, kai ne kullum zuciya da cin zalin yan uwan ka, duba kiga yanda ya fasawa d'an uwanshi fuska, shi kuma wannan daga rabo ya fasa mishi baki, meye anfanin haka dan Allah? To wallahi na daina yarda daga yau, yanda yake jin haihuwarshi akayi a gidan nan haka suma yaranmu haihuwarsu mukayi, kuma nak'uda bata fi nakudaba bare yace uwarshi ta fi mu shan wahala, dan haka wallahi daga yanzu ni zan dinga tarewa kai na fad'an tunda dai shi mugu ne na gidan gaba." Wannan b'ab'atun ne yasa Hajia Husseina fitowa daga d'akin ta, Soueba ce tace "Dan Allah Zeinabu kiyi hak'uri, da Ammar da Junaid ai duk d'aya ne a gurinki kamar 'ya'ya suke a wajenki, dan sun samu sab'ani bai kamata ace muna jin zafi haka ba, yan uwane su kuma mabiyi da mabiyi, dole dama ana samun haka saboda zaman tare, amma bai kamata ki dinga fad'in haka a kan shi ba." Hajia Husseina ce tace "Lafiya ku kuma meke faruwa ne?" Zeinabu ce tace "Hajia, Ammar ne ke fad'a da Amar, Junaid daga zai raba kawai ya samu shima ya bubbuge shi saboda fin k'arfi, shine yanzu nake magana Soueba take nuna min ba hakanan ba, to dan Allah yanzu su Ammar yara ne da za ace har yanzu suna fad'a? Sanda sukayi fad'an k'uruciyar wa ya tab'a cewa wani abu, ko da suna yara ma kullum shine ke saka mana yara kuka, kuma yanzu ace sun girma ma ba zasu huta daga kaidin shi ba saboda shi ya zama wani shaid'an." Murmushi Husseina tayi tace "Ai gaskiya Soueba ta fad'a, ba kina kwaroronton sun samu sab'ani yanzu ba? To zuwa gobe ko jibi a falon nan zaki tarar da su kuma suna wasa tare kamar lokacin da suke yaran, kuma kema kin sani ko wasa suke sunfi tsokanar Ammar d'in, amma shi ko magana bai cika son yi ba, kenan meye abun wannan fad'an?" Amar da yana shiga d'akin ya samu Ummy zaune kan kujerar coiffeuse (dressing miror) zunbur ta mik'e tana kallonshi ta nuna mishi k'ofar fita tana fad'in "Fitar min a d'aki Amar, fita." Cikin muryarshi ta shan wahala ga dishi-dishin da yake gani yace "Ummy kiyi hak'uri na fad'a miki ab..." Cikin tsawa tace "Ka fad'a min me Amar? Me zaka fad'a min? Shin Amar tun yaushe nake fad'a maka ka dinga hak'uri da halin d'an uwanka? Sau nawa ina fad'a maka kai da shi akwai banbanci na hallaya ka dinga kiyaye b'acin ranshi? Amar na fad'a maka kai ne d'an uwanshi wanda ko bayan ba ranmu zaka iya tsaya mishi duk da shine babba, me ya sa ba zaka dinga hak'uri ba da duk maganar da zata fito daga bakinshi? Tunda kafi kowa sanin halinshi magana indai har ta zo bakinshi ko ni uwarshi fad'a min yake bare kuma wani, amma ku tsaya kamar yara yan shekara biyar wai kuna fad'a, fad'a Amar da girmanku da komai? Amar so kuke duk gidan nan na zama mujiya ko kuma kamar wacce ta haifi annoba?" Komawa tayi ta zauna cike da damuwa kamar zata fashe da kuka, cikin sanyin jiki da rashin jin dad'i ya durk'usa kusanta ya rik'e k'afar ta yace "Dan Allah Ummy kiyi hak'uri ki yafe mana, wallahi har cikin raina bana jin dad'i na ga kina damuwa akan halin Ammar, Ummy in kina damuwa da halinshi hakan zai iya janyo mishi fushin ubangiji, kiyi hak'uri dan Allah ki daina Ummy, nayi kuskure dana kula shi, amma na miki alk'awari hakan ba zata sake faruwa insha Allahu." Hawaye ne suka taho mata ta d'ora kanshi a saman cinyarta ta kasa cewa komai, ita yanzu babban tashin hankalinta idan Hajia ta zo ta ga Amar da wannan ciwon a fuska, tashin hankalin zai fara ne idan aka ce Ammar ne ya dake shi, _kowane d'an adam da wanda Allah yake jarabtarshi da son shi, Hajia ita ta ta jarabta Amar ce, duk cikin 'ya'ya da jikoki babu wanda Hajia ke nunawa k'auna kamar Amar, babu wanda take nuna damuwarta a kanshi kamar Amar, takai ta kawo Amar na iya mata magana kan wani hukunci data yanke kuma ta janye shi, tun yana yaro yake samun kulawarta da soyayyarta, hatta yayesu da za ayi ita ta amshi Amar hannunta, kuma sun fara samun rashin jituwa ne da Ammar saboda kullum shi ke nasara akan Amar in dai ana fad'a, da kaji Amar na kuka to Ammar ne ba makawa, ita kuma saita dinga wa Ammar fad'a tana nuna mishi tsana a fili, hakan yasa shima baya wani k'aunar ta bare al'amuranta,_ to wannan ne yanzu damuwarta dan tasan sai rai ya b'ace fiye da yau, tana cikin wannan tunanin suka ji muryar Zeinabu na wannan fad'a, cikin sanyin murya tace wa Amar "Ka ji ko, na tabbata suna magana ne akan abinda ya faru." Mik'ewa Amar yayi yace "Ummy ni fa bana jin dad'i na ji ana fad'an maganganun marasa dad'i akan d'an uwa na, zanje na fad'a musu kar wanda ya damu da abinda ya faru yanzu, tsakaninmu ne wannan kuma zuwa anjima zamu shirya." Rik'e hannunshi tayi tace "Bara na duba maka ciwonka tukuna." Zage hannunshi yayi yace "A'a Ummy zan dawo yanzu, kinsan tanti (Zeinabu)da ji-nini." Mik'ewa tayi ita ma ta bi bayanshi, suna tsaye lokacin Husseina ke tambayar lafiya? Duk abinda ta fad'a akan kunnensu, Amar zai tafi wajenta Ummy ta rik'e shi, tana cikin wannan fad'an kuma sai ga Ammar ya shigo falon da takonshi na k'arfi kamar zai tashi k'asa. Tunda ya koma b'angaren su tunanin Ummy ya dameshi yasan yanzu tana can tana kuka, shiyasa ya tashi yayi wanka ya canza kayan jikinshi zuwa wata shadda ruwan k'asa ya fito, tunda ya doso falon ya ji wannan hayaniyar ya sake tamke fuska kar ma aga damarshi, Zeinabu na fad'in "Ai dan ya ga wuri ne shiyasa yake mana iskancin son ranshi, suma ba dan suna wasu sakarkaru ragwaye ba har yaushe mutum kamarku wanda duk cikinsu babu wanda ya bawa wata biyu da haihuwa amma ku tsaya yana lallasaku son ranshi." Husseina dai murmushi ne nata tace "Zeinabu ai abun a jini yake, tun daga yanayin tafiyarsu zaki duba, zaki fahimci ko a tafiya shi da k'arfi yake tashi sab'anin su." Tsaki tayi tace "Ala wadaran naka ya lalace, to badan basu da wayo ba ai ko taron dangi ne su mishi wata rana su jijjiga shi shima ya ji jikinshi, wallahi sai kiga an zaunnnn..." Gimtse bakinta tayi dan har ga Allah ta tsorata kuma gabanta ya fad'i lokacin data d'ora idonta akan Ammar daya had'e fuska yake kallonta ido jawur kamar kullum, Ummy da suke k'ofar d'aki tsaye tasan sai yayi magana, dan haka daga can tace "Ka wuce ka tafi inda za ka." Amma ko kallon Ummy baiyi ba kuma har yanzu bai daina kallon Zeinabu ba yace "Idan kina ganin zasu iya ki basu shawara mana tunda kun shirya rasa 'ya'yanku." Saida Ummy ta lumshe ido, dan tasan dama sai anyi haka, shi fa in dai maganar zata zo to sai ya fad'a ko za'a yanka shi, babbar matsalar kuma shine bai damu da girman wanda zai fad'awa ba ko kuma d'acin maganar ko rashin dacewarta, zai fad'a ne in ya so kai kayi kuka dan bak'in ciki, ko kuma ka zage shi kayi tir da halinshi shi duk d'aya ne a gun shi, takawa yayi ya nufi wajen Ummy tana ganin haka ta shige d'aki ta rufe k'ofar da makulli tana wani sabon kukan, k'ofar d'akin ya tsaya yana kallon fuskar Amar da tayi jina-jina, wani irin buga k'ofa ne yayi d'aya biyu baiyi na uku ba sannan yace "Kiyi hak'uri fa ki daina kuka, kinsan zai iya ja miki ciwon kai, daga haka kuma ake kamuwa da hawan jini ko ciwon zuciya, kina so ne ace zan nuna k'warewata na zama likitan zuciya a kan ki?" Yana fad'in haka ya juya zai bar d'akin, cak kuma ya tsaya saboda duk baya jin dad'in ganin Ummynshi na kuka saboda shi, d'an uwan shi kuma na fitar da jini a dalilinshi, juyowa yayi ya kalli Amar dake shirin bubbuga k'ofar d'akin, sake d'auke kai yayi kuma wata zuciyar na fad'a mishi ai sai ya d'auka ka damu da shi ne, a hankali ya lumshe ido ya sauke numfashi a zuciyarshi yace "Ka damu da shi mana Ammar, ku fa ko a cikin ciki tare kuka rayu, ka d'auka kai da shi kamar kuna rayuwa ne da rai d'aya." Bud'a ido yayi ya sake kallon Amar wanda shi ma yake so ya ga sun shirya ko dan mahaifiyarsu ta ji dad'i, kamar baya son maganar haka ya motsa bakinshi yace "Muje na wanke maka ciwonka." Da sauri ya k'araso kusanshi ya rumgumeshi dan sam bai d'auka Ammar zai fara mishi magana ba, sosai yake ta k'ara cakume shi saboda k'auna, amma me Ammar zaiyi sai kawai ya raba kanshi da shi ya had'e rai yace "Miye haka malam sai ka b'ata min kaya da jini, muje ni dallah." Da k'arfi ya juya ya fita Amar ya bi bayan shi yana girgiza kai, lallai a duniyar nan in har shi ya kasa fahimtar d'an uwanshi to babu mahalukin da zai iya fahimtarshi bayan wanda ya halluce shi, Husseina da Soueba da dariya suka bisu har Husseina na fad'in "Kin gani ko Zeinabu, shiyasa shiga fad'an yara ke da kunya wallahi, dan Allah ki daina damuwa da rayuwarsu, mu yarda cewa haka Allah ya hallici Ammar." Tab'e baki tayi tace "Hum! Ni bana so na ji kuna cewa wai yara, yaran nan fa ba dan dogon karatu da sukayi ba wallahi da yanzu sun aje mana jikoki bibbiyu ko sama da haka." Dariya Zeinabu tayi tace "Gashi kema kin fad'a kince yara." Shigowar Junaid cikin sabon shiri yasa suka kalleshi a tare, shima dai fuskar nan a had'e take dan ranshi ya b'ace sosai, Jamil ya kalla wanda ke zaune yana latsa wayarshi yace "Kai in za ka je ka taso mu tafi." Mik'ewa ya yi yace "Mu tafi kawai." "Ina kuma zaku je?" Cewar Husseina, a tak'aice Jamil yace "Gidan roumji." Zeinabu ce tace "Inda ubanninsu suka tafi zasu je, amma babu wanda zai iya fad'a mana dalilin zuwa." A motar Junaid suka d'auki hanya ba ko waiwaiye saboda su isa da wuri, Ammar ma wani d'aki suka shiga wanda ya ware yake zuba duk wasu kaya da suka shafi na jinya, sannan har magunguna ke akwai da kayan aiki masu mahimmanci wanda babu su a ma k'asar baki d'aya, hakan yasa baya wasa wajen kula da su, zaune Amar yayi kan gado Ammar yasa k'aramin almakashi da k'ada da yan ruwan kashe ciwo yana goge masa, babu mai kallon idon wani bare magana, saida ya gama ya duba inda ke buk'atar a rufe yasa k'aramin bandeji ya rufe mishi, ba tare daya kalleshi a yace "Kana jin jiri?" Saida ya d'an dafe kai yace "Eh, dan da k'yar ma na kawo kaina nan, na so na ce ka goye ni amma kuma..." Kallonshi yayi yace "Amma kuma me?" "Kana hushi da k'aninka, d'an uwanka, shak'ik'inka, sannan abokin rayuwarka." Duk yayi maganar ne cikin marairaicewa, k'ala bai ce masa ba sai ma wasu kwalaye dayake fito da su yana son d'auko wani magani, ya sha wahala kafin ya d'auko ya bud'e ya d'auki wanda yake buk'ata ya mayar da sauran, fitowa yayi daga d'akin jim kad'an ya dawo, ruwa ya bashi a roba tare da maganin yasha, d'aya maganin kuma ya sa a cikin kofi da ruwa, saida ya gama tafasa ya mik'a mishi ya shanye ya aje kofin, ba tare daya kalli fuskarshi ba yace "Ka kwanta kan gadon nan." Ganin ya juya zai fita yasa Amar cewa "Har zuwa wane lokaci?" Ba tare daya juyo ba yace "Har a busa k'aho." Murmushi kawai Amar yayi shi kuma ya fice, yana fita kuma motar shi ya fad'a ya tayar, mai gadi na bud'e k'ofa ya suri motar yayi waje, hanya ya d'auka shima kamar zai tashi sama, shi ma dai kamar su Junaid hanyar gidan roumji ya nufa, sai dai duk gudunshi bai iya riskar su Junaid ba dan sun rigashi d'aukar hanya kuma suma gudu suke sosai. *K'arfe* 06:20 na yamma Amar ya fito cikin shiri ya samu Ummy ya mata sallama yace zai tafi shima k'auye saboda kar ran Abba ya b'ace, cike da damuwa tace "Amar kayi hak'uri mana zuwa gobe sai mu tafi tare, tunda kaga ba lafiya ne da kai ba." Dariyar gefen labb'a yayi yace "Haba Ummy lafiya ta lau fa, ki bari naje kawai kar Abba ya ga kamar bamu ji maganar sa bane, kuma kinga dukansu fa ina kyautata zaton can suka tafi, kinga gwara nima na hanzarta na tafi ko da ana sallah magriba ne saina isa." Cikin sanyi tace "Shikenan Amar, Allah ya tsare ka ya kare gabanka da bayanka." Murmushi yayi sosai yace "Ameen Ummy, sai mun dawo." "A dawo lafiya." Ta fad'a tana binshi da kallo harya fita. Yana fita su Hamna na shigowa da motonsu dan saida suka kai d'inki sannan suka dawo gida, haka ma ba jimawa Umaima ta shigo gidan tare da drebanta, sai Jamila da ta shigo gaf da magrib daga école. *Gidan roumji* Rana ta fad'i sosai su Junaid suka iso, tunda suka fito daga mota lieutenant da colonel ke kallonsu da mamaki, k'arasowa sukayi cikin mutane suka gaishesu da girmamawa tare da musu ta'aziya, sun shiga cikin gidan dan yiwa na cikin gida suma sai ga motar boss ta karyo kwana, da k'arfi ya ci burki ya kashe motar ya fito makulli da waya a hanu, ga kyau ga kyan tsari da hallita sai dai a wurina babu kyan hali, da k'akk'arfar tafiyar nan tashi ya k'araso yana sallama amma fa wanda yayi sa'a ne kad'ai ke ya ji sallamar dan kamar bai so yayi ba, saida yayi zaune ya tank'washe k'afafun shi kafin ya fara bawa na kusa da shi hannu, colonel kam daya tsura mishi ido a ranshi cewa yayi "Lallai yaro na, wannan da ace kai général ne na soja da anshiga uku, ko mu dake iyayanka dai saida muka gaishe da mutane kafin muka zauna saboda wurin mutuwa ne, amma kai sai bayan ka zauna kake gaishe da wanda ke kusa da kai, humm." Lieutenant kuma haushin Ammar ne d'in ya kusa kashe shi shiyasa ma ya d'auke kallonshi daga kan Ammar d'in dan kar zuciya ta kwashe shi ya mareshi, yana gama tashi ta'aziyar ya fara danna waya, da sauri Labaran ya kalleshi yace "Ammar ka shiga ciki mana ku gaisa da matan." Kallonshi yayi lokaci d'aya kuma ya mayar da kallonshi kan wayar, yana kallon wayar tashi ya mik'e yasa takalminshi ya nufi cikin gidan a ranshi yana fad'in "Yanzu mutum na shiga zasu saka maka ido suna kallo, kowace burinta ka mata magana ta ji dad'i, mtssss, shiyasa na tsani shiga irin taron nan." *Ikon Allah sai kallo, to Ammar me ka d'auki matan? Sai kace wasu tsofaffin...*😏 Yana kallonsu su Junaid suma suna kallonshi haka kowa ya gama ya fito, suna zuwa kuma wasu har sun nufi masallaci wasu kuma na alwala, suma alwala sukayi suka nufi masallacin, tare sukayi sallah suka fito, fitowar lieutenant da colonel yayi daidai da shigowar Amar cikin kwanar, lieutenant a ranshi yace "Wato yaran nan sun raina mutane ko? Amma laifin duk na waccen babban kwabon ne." Tsaye yayi hakan yasa colonel ma tsayawa, su Junaid da Ammar na fitowa lieutenant yace su zo, Amar na ganinsu saboda ya hasko fitilar motarshi ya tsaya wajensu ya fito, cikin girmamawa yace "Abba ina wuninku, har kunyi sallah ko? Bara nima na yi alwala." Zai wuce lieutenant ya dawo da shi baya ya kallesu dukansu yace "Wato da na ce ku taho gaba d'aya shine kowa yayi gaban kanshi, yanzu ribar me kuka ci da kuka nunawa mutane ku kanku ba had'e yake ba?" Shiru sukayi dukansu suna kallon k'asa sai boss da idonshi ke kan wayarshi yana latsawa ya rumgume hannu d'aya, juyawa lieutenant yayi ya kalli Ammar d'in da ya ga ya mayar dashi wani d'an iska ma, wani haushi ne ya kashe shi sai kawai yasa tafin hannu ya bangaji k'eyar Ammar, bai ankara ba yaji bugun dan haka ya juyo ya kalli mahaifin nashi, had'e fuska yayi ba alamar wasa yace "Abba meye haka? Kai baka san cewa kai shine mutum ba? Duk wani abu mai mahimmanci a cikin k'wak'walwa yake, so kake kasa na rasa komai nawa?" Hannu ya d'aga da nufin sake mazgeshi colonel yayi saurin rik'e hannunshi yace "Ba kamata yayi ace ka fara tambayar meya faru ba kafin duk wannan b'acin ran, ko baka kula da fuskar Amar bane, sannan ka dubi Junaid ma, baka tunanin ko wani abu ya samesu a hanyar?" Fizge hannunshi yayi yana kallon Ammar yayi k'wafa kafin ya kallesu yace "To naji, wa zai fad'a mana meya faru?" Shiru sukayi sai wuk'i-wuk'i da ido da sukeyi, Labaran ne ya kalli Jamil yace "Kai ba tambayarku ake ba kuka mana shiru?" Jamil kam kallon Ammar yayi wanda ya ga ya kalleshi, idonshi kad'ai suka fassara mishi manufar kallonshi, dan haka ya ja baki yayi gum saboda tsoro, sai dai ya manta gaba da gabanta, colonel ne cikin tsawa yace " Wai ya ana muku magana kuka mana shiru? Shin ku yan mata ne bare ku d'auka son ku muke." Wani kallo Ammar ya mishi yace "Idan ma yan mata ne mu sai mu tsaya muna sauraron tsofaffi irinku." Labaran kam bushewa yayi da dariya inda lieutenant ya zabura zai bugeshi Labaran d'in ya rik'e shi, cikin dariyarshi yace "To ai gaskiya ya fad'a, tsofaffin ne mu mana." Kamar daga sama suka ji saukar mari ji kake "Tauuuuuu." Da sauri Junaid ya dafe kunci saboda wani mahaukacin mari da colonel ya watsa mishi yana fad'in "Iskanci kai, ana muku magana zaku d'auke mu wasu shashashu." Lieutenant ne yace "Meye haka saboda Allah? Yanzu shine kenan yayi laifi a wurin nan? Me ya sa ba zaka mari wannan ba dake kusa da kai yana mana shak'iyanci sai wannan? Saboda a ganinka wannan ne ka haifa su kuma wad'annan duk 'ya'yan yan uwanka ne, mtsss." Lieutenant Jamil ya kalla ya zaro ido yace "Yanzu zaku fad'a mana meya faru da har yasa ku ka k'i bin umarnin dana baku na a taho tare?" Cikin rawar murya Jamil yace " Dama da zamu..." Karaf Amar ya karb'a da cewa "Ni ne fa na samu had'ari akan moton wani abokina, shine da na zo gida sai aka ce su Junaid su taho saboda Ammar shi ya duba min ciwon, bayan Ummy ta zo gida kuma sai shima suka ce ya taho, ni kuma ganin duk sun taho yasa na kasa hak'ura na taho." Colonel ne ya kalli Junaid yace "To kai kuma uban wa ya ci uwaka a bakin na ka?" Bawan Allah Junaid sai lokacin ya d'auke hannu daga kuncinshi yace "To ni kuma waye zai dake ni a baki ina d'an soja guda." Jinjina kai yayi yace "Da kyau to tunda kana tuna hakan." Mayar da kallonshi yayi kan boss da ke harkar gabanshi kamar baisan sunayi ba ya kamo hannunshi yace "Soja d'an soja muje ko." Wucewa sukayi inda suma suka bi bayansu lieutenant na jin haushin colonel saboda sam baya ganin laifin Ammar, zaka iya cewa ma yafi nuna mishi k'auna fiye da Junaid da kuma Umaima da Jamila. Bayan sunyi sallah isha'i aka fito da abinci aka ci, lokacin ne suka fara haramar komawa gida dan sun fahimci kwana anan ba zai musu ba, har cikin gida suka samu Hajia suka fad'a mata, sam Amar bai yarda ya had'u da ita ba dan saita tambayeshi meya same shi, ita kuma k'aramin aikinta ne ta musu bala'i a gidan rasuwa, da k'yar ta yarda zata kwana dan cewa tayi zafi kasheta zaiyi kafin safiya, saida Alhaji yasa baki yace shima zai kwana anan dan bai dace ta bar wurin ba daga yanzu har zuwa kwana uku, haka dai ta hak'ura amma tace ba tayi alk'awarin zama har sadakar uku ba, nan suka juyo dukansu sai Hajia da Alhaji acan, ba tare da wata matsala ba Allah ya kawosu gida lafiya, kowa wajen na shi iyali ya nufa ya samu yayi wanka, k'arfe *10:00* na dare lieutenant Hassan da colonel Hussein da Labaran suka hallara kan babban teburin cin abinci, in dai har suna gari dama sukan had'u ko dan su tattauna matsalar data shafesu, Soueba ce yau take zuba musu duk abinda zasu ci, tana cikin zuba musu ruwa da lemu ta kalli mijinta Labaran tace "... *Mu had'u a shafi na gaba insha Allah.*✋ *Allah ka mana kyakyawan k'arshe*👏 27/05/2020 à 14:46 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 *😂 Nasan za ku sha mamaki sosai ganin na dawo da ci gaban sanin masoyi, to ku kwantar da hankulanku kusha kallo kawai, duba da akwai wasu abubuwa daya kamatain ace an warwaresu tun a na farko, amma Allah bai nufa ba sai yanzu idan ya ara mana rai da lafiya, insha Allahu abun zai k'ayatar da ku fiye ma da na farko, kuma wannan shi zai zama na k'arshe da yardar Allah.* _Bismillahir rahamanir rahim_ _1_ _Idan masu karatu basu manta ba mun tsaya a waccen labarin *Sameera* na da ciki na wata biyar, sannan Abbas na shirin had'a *Raihan* aure da *Abdul* d'an wajen Abbas mai biwa *Husnah* da zaran ta kammala secondary d'in ta, to zamu d'auki labarin daga bayan haihuwar Sameera muyi gaba insha Allah._ *Abbas* ne zaune tare da Abba (mahaifin Sameera Mus'ab) da kuma Umma (mahaifiyar Abbas Falmata) a gefensu, cikin hushi Abba yace "Ina! Wannan ma maganar banza ce, wallahi ba zan tab'a bari ku had'a *Raihan* da tsatson wannan mutumin ba, *Abba*? Ina! Ba dai d'an Abba ba wallahi, mutumin daya cutar da kai ya cuce mu gaba d'aya." Cikin taushin murya da nutsuwa Umma tace "A gaskiya nima abin bai kwanta min a rai ba, kuma naga ma du-du-du yaron shekararshi nawa? Bai ko gama mallakar hankalin kanshi ba, sannan ita kanta Raihan d'in nawa take da har zaku fara maganar aurar da ita? Shekara goma fa, ba kwa tunanin ku zo ku tsayar da magana akan ga wanda za'a bata, a k'arshe zuciyarta ta kamu da son wani kuma ba shi ba, tunda zata ci gaba da zuwa makarantarta ai." Abba ne yace "Wannan ma abun dubawa ne, irin wannan had'in tun da k'uruciya yana da matsala gaskiya, bansan me kuka gani ba da har kuke tunani had'a su." Cike da kulawa *Sameera* ta kalleta tace "Hakane Umma, amma ai ba yanzu za'a musu auren ba, sai nan da shekara hud'u, kunga a lokacin ya samu cikakkiyar shekara ashirin da uku, ita kuma ta koba komai dai ta zama balagaggiya, sannan ba zamu had'a su bane haka kawai, zamu fara tambayar ra'ayin du akan lamarin." "Yanzu in banda abinki *takwarata* ina Raihan ina wani sanin so? Ko ta amsa miki da eh wallahi idan ta mallaki hankalin kanta zata iya canza magana, 'yar shekara goma fa ake miki magana ba 'yar sha shida ba ko sama da haka." Cikin tafasar zuci Abba yace "Kunga, ni ba k'arancin shekarun yaron bane damuwa ta, tunda ko yanzu aka mishu aure za'a samu kyakyawan sakamako daga gareshi ta hanyar zuri'a, kuma idan da shak'uwa da fahimta duk wannan ba matsala bace a tsakaninsu, kawai dai yaron ne bai min ba saboda kasancewarshi d'an mak'iyina." A hankali *Abbas* ya d'ago ya kallesu cikin nutsuwa da girmamawa yace "Abba, Umma, sam banyi tunanin wannan maganar zata iya rasa muhalli a zuk'atanku, Abba, ko fa ubangijin daya hallicemu baya kamamu da laifin da waninmu ya aikata, ina ganin kamar rashin adalci ne da kuma dacewa ace zamu hukunta *Abdul Malik* akan laifin da mahaifinshi ne ya aikata, duba da lokacin da abun ya faru ko kanshi bai sani ba, namiji ne shi ba kuma lallai yayi halayyar mahaifinshi ba, zamu iya cewa mu shaidane akan hallayarshi, bai kamata mu hanashi auren Raihan ba in har suna son junansu, ko 'yar uwarshi *Husna* ta samu miji tayi aure a dalilin rabin rayuwarta da tayi a gidan nan, ni da hannu na na bayar da aurenta Abba, shin kuna ganin ya kamata ace mu mun hana auren d'an su da 'yar mu saboda tunanin abinda mahaifinshi yayi? Bai dace ba hakan iyayena, kuyi hak'uri ku sawa yaran nan albarka, hak'ik'a idan kuka ce baku yarda ba za'a fasa dole, amma hakan ba zai mana dad'i ba." A hankali Sameera tace "Gaskiya ne Abba, kuma na ga ko shi kansa Abban ai mun yafe masa laifin daya mana, kuma kuyi hak'uri ku yafe masa sannan ku manta da baya, duba da mutumin nan yanzu baya raye a doron duniya." Kallon juna Abba da Umma sukayi kafin Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Shikenan, mun amince, amma abisa wani sharad'i guda d'aya." Sameera ma da Abbas kallon juna sukayi kafin Abbas yace "Wane irin sharad'ine wannan Abba?" Ba alamar wasa yace "Sai in kun amince za'a yi wa yaron gwajin cuta mai karya gwarkuwar jiki da ma sauran cututtuka masu had'ari wanda akan iya d'auka ta hanyar mu'amula." Dafe kai Abbas yayi yana tunani, yasan halin gogon nasu in har basu amice ba to za'a fasa ne, dan haka ya d'an kalli Sameera wacce ita ma take kallonshi kafin ya kallesu yace "Shikenan Abba, mu ma mun amince." "Shikenan, Allah ya tabbatar da alkairi." Cewar Abban, da "Ameen." Suka amsa da shi. Sai Abba daya mik'e zai fita daga falon yana fad'in "A dole wai sai an raba mutum da matarsa, ni ina son amaryata amma kuke son saita min kishiya." Dariya sukayi sai Umma da tace "Shi ya sa zanfi kowa farin ciki idan haka ta kasance, dan ko ba komai na rabu da kishiya d'aya." Suma mik'ewa duka sukayi suka nufi b'angaren nasu Abbas, masha Allah falon ya had'u iya had'uwa, gashi duk yaran dake d'akin kowa harkar gabanshi yake amma cikin nutsuwa, sai Raihan dake zaune kan kujera da littafi tana karatu, sai kuma Abdul dake gefe tare da k'aninshi *Jabir* suna danna wayoyinsu, duka zaune sukayi kafin Sameera tace "Ku tashi kuje ku kwanta dare yayi." Kusan duka yaran suka amsa da "Ok Ammie." Mik'ewa sukayi inda kowa ya nufi nashi d'akin, Raihan ma tashi tayi sai Sameera ce tace " *Mamana* zo nan." Cikin sanyi jiki da nutsuwa wanda ya zama halitar yarinyar ta taho ko kallon idon mahaifiyarta ba tayi ba harta zaune kusa da ita, Abdul ma da Ameer zasu mik'e Abba yace "Kai Jabir kaje, Abdul ka zauna zamuyi magana." Cikin tsananin fad'uwar gaba da fargaba ya zame ya zauna k'asa duk da Abbas yace ya zauna inda yake, shiru falon ya d'auka kafin Abba yace "Abdul, abinda yasa nace ka zauna dama ba wani abu bane, ni da iyaye da kuma mai sunan Mamana (Sameera) munyi wata shawara akan ku kai da Raihan, kunsan ance abinda babba ya hango yaro ko ya hau dutse ba zai hango ba, to duba da hakane yasa muka fahimci kamar da wani abu tsakaninka da Raihan, shi ya sa na ce bara mu tambayeku muji ko kuna son junanku?" Tsaro ne matuk'a ya bayyana a fuskar Raihan duk ta zaro ido, yayin da Abdul zufa ta fara tsatsafo masa saboda jin abun banbarak'wai, wasu kirce-kirce ya fara ya rasa amsar da zai bayar, hakan yasa Abba cewa "Ka yi magana mana Abdul, ba za'a tauyeka ba ai." Shiru ya sakeyi gabanshi na fad'uwa, Abbas ne yace "Abdul." A hankali ya d'ago yace "Fad'a min gaskiya, kana son Raihan?" Raihan da taji abun wani iri tashi tayi da gudu ta haura sama ta shige d'akin ta suna kallo, murmushi Sameera tayi kafin tace "Ita ta amince, saura kai." Shima yunk'urawa yayi cike da kunya da murmushi ya nufi d'akinsu da suke sauka idan sun zo nan, Abbas ne yace "Bamu fahimci komai ba Abdul, hakan na nufin ka amince kenan?" Juyowa yayi cike da kunya ya d'an jinjina kai alamar eh, da sauri ya k'arasa sama shima ya bi kusurwar da zata sadasu da na shi d'akin, Abba ne ya kalli Abbas yace "Amma ya kuka barshi ya tafi baku fad'a mi shi sharad'in ba?" Abbas ne yace "Abba karku damu da wannan, na muku alk'awarin kawo muku sakamakon gwajin Abdul nan da kwana biyu insha Allahu." "Shikenan Allah ya yarda." Suka amsa da "Ameen." Umma da Abba b'angarensu suka koma inda Abbas ya wata kusurwar wacce ka d'auka wani sabon gida ne a ciki, sai Sameera da ta haura sama ta shiga d'akin Raihan, tsaye ta sameta ta saka kayan baccinta tana caje gashinta, zaune tayi bakin gado harta juyo ta kalleta tace "Ammie ke ce?" Murmushi kawai ta mata, takowa tayi ta zo ta zauna tana turo baki gaba cikin shagwab'a ta rik'o hannun Sameera tace "Ammie, wai akan me Dady yake magana ne?" Murmushi sosai Sameera tayi tace "Wai baki fahimci me yake magana akai ba? Kee 'yan matana fad'a min gaskiya kedai." K'ara had'e rai tayi tace"Ammie, da gaske na ke fa." Shafa kanta Sameera tayi tace."To in tambayeki mana? Tsakani da Allah Abdul baya birgeki?" Saida ta juya idonta kafin tace "Ammie, yana birgeni mana, kamar yaya na d'auke shi fa." Tana ci gaba da shafa kanta tace "To ba kya jin wani abu a game da shi a zuciyarki? Misali idan kin ganshi, ko kuma yayi nesa da ke?" B1 tare da sanin mahimmancin abinda take tambayarta ba tace "Ammie ba na jin komai, kawai dai ina sonshi a matsayin yayana." Kallon fahimta ta mata sosai tace "To kina ganin zaki iya aurenshi? Ma'ana zaki iya yin rayuwar aure da shi ta har abada?" Ido ta d'an zaro tace "Ammie, irin rayuwar da kuke da ke da Dady? Da kuma Mammy da Papy?" Saida ta kama kumatunta tace "Good girl, haka na ke nufi." Dariya ta bushe da ita ta fad'a k'irjin Sameera ta rumgumeta tana fad'in "Ammie ni kunya nake ji, bana so na yi aure na barku, ina so na ci gaba da zama da ku a gidan nan." Sosai ta rumgumeta tace "Hakan na nufin Mamana ta amince kenan?" K'ara tusa kanta tayi a k'irjin ta ba tace komai ba, dan haka ta d'ora da "To karki damu, indai kina son zama tare damu ai abune mai sauk'i, Dadynki zai iya ware muku part na musamman." Kunya ce tasa Raihan tashi ta shiga toilet da gudu, binta tayi da kallo kafin ta mik'e tace "Ni na tafi saida safe, ki fito ki kwanta ke ma." Daga toilet d'in ta amsa da "Good night Ammie." Saida ta shiga d'akin sauran yaran duk ta samesu sukayi saida safe kafin ta wuce nasu sashin, saida sukayi rigima da Abbas kafin ta yarda ta kai Ameer wajensu Ammie ya kwana, dan cewa yayi wani cikin zai mata dan yana so tayita haihuwa, haka fa rayuwar gidan nasu take tafiya ba tare da tunanin wata rana bak'in ciki zai iya ziyartarsu ba, ta b'angare d'aya kuma maganar Abdul da Raihan na nan daram, sai dai har yanzu Abbas bai iya maganar gwajin da za'a wa Abdul ba saboda yana ganin rashin dacewar hakan, su Ammie kuma basu sake mishi maganar ba tunda ba abu bane na gaggawa, sai dai kuma Raihan kunyarta tayi yawa sosai ta yanda har yanzu ba wata shak'uwa bace tsakaninsu, dan ko tana zaune a wuri ya zo tashi take da kunya da nutsuwa ta bar wajen, Fadila da Ma'awa kad'ai suke sakewa dashi suna hira amma ita tana jinsu, duk da dai a zuciyarta tana jin yana birgeta, amma bata iya nuna mishi, idan ya koma gidansu ne kad'ai tafi sakewa da walwala, ta b'angare d'aya kuma suna karatunsu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, yan watanni kad'an Abdul ya kammala secondary d'in shi Abbas ya turashi jami'ar madina, bayan wani lokaci kuma Jabir kuma shima ya kammala nasa inda ya zab'i yin karatunshi a jami'ar Ahmadu Bello, shima babu wata matsala da yake fuskanta saboda yana tare da magajiyar mahaifiyarsu *Safeena*, kwana tashi babu wuya a wurin Allah sai kuwa su Raihan suma suka samu shiga secondary. *Bayan shekara hud'u* sai gashi Raihan Fadila da Ma'awa sun fara jarabawa ta zangon k'arshe a ajinsu, lokacin fa masha Allah yan mata an girma sosai kowace hallitarta ta fara bayyana ta zama budurwa yar shekara sha-biyar, musamman Raihan wacce tayi k'aramin jiki kamar na Sameera sai tsayi wanda ya dace da ita, ga farar fatarta ta gama bayyana kyau da shek'i, haka ma dogon gashinta wanda yafi ma na uwarta, domin kuwa ita tun tana yarinya ana gyara mata shi sab'anin Sameera data girma a k'auye, sam bata da wadatar k'irji dan kusan Raudat dake k'anwarta ta biyu ma kuma ko balaga batayi ba har nonuwanta sun kusa na Raihan d'in, lik'e suke a k'irjin ta sosai ba su da wani girma na azo a gani, dama idan Allah ya hanaka wani abun saiya baka wani abun, kamar yanda take da shafaffen ciki mai fad'i haka k'ugun ta yake a bud'e, kuma masha Allah tana da mazaunai daidai gwargwado, k'irarta abar birgewa ce da d'aukar hankalin maza, kamar yanda mahaifiyarta take haka ita ma take, gashi dama Sameera har yanzu ba wata k'iba bace tayi shiyasa ma idan kaga fuskokinsu sai kace wata yaya da k'anwa ne, yanzu haka sun kammala jarabawar sakamako kawai suke jira sai islamiyya da suke zuwa, ba jimawa kuma Abdul shima ya dawo daga madina hutu dan *doctor* yake sha'awar zama na musulunci, a yanzu ne kuma Abbas ya fara tunanin yi mishi gwajin jinin, amma rasa hanyar da zaibi yasa ya shirya shawartar su Bashir da Naseer. *K'auyen Gwagwa* *Harira* ce ta fito cikin shirin tafiya birni ita da yayanta, *Baaba mai wake* (k'anwar mahaifiyarsu) ce ta k'are musu kallo kafin ta tab'e baki tace "Tafiyar ce zakuyi?" Harira ce ta amsa da "Eh Baaba, zamu tafi sai mun dawo." Sake tab'e baki tayi tace "Humm." Juyawa sukayi sai yayanta daya fito da naira d'ari a aljihu ya bata yace "Baaba ga wannan, idan su *Karime* sun taso daga islamiyya saiki basu wake dashi." Nan ma dai sake tab'e bakin tayi tace "Yanzu d'ari ce zata isa su ci abinci su k'oshi? Kasan su da shegen cin tsiya fa." Cikin taushin murya yace "Kiyi hak'uri Baaba, kud'in mota kad'ai suka rage mana anan, suma wallahi aro su nayi wajen *Halidu* mai tebur, ko na abinci ba zamu samu ba." Cikin jin haushi tace "Naji dan Allah, ca-ca-ca-ca kamar carbi ta tsinke, kuje sai kun dawo." Mik'ewa tayi ta nufi wajen bisashen da take kiyo tana fad'in "Ba gaira ba dalili na d'auko wa kaina jaraba, shegen jaraabben son kud'in iyayenku ne ya ja muku ai, yanzu gashi a banza a wofi suna d'aure a magark'ama suna neman k'are rayuwarsu can, jaraba kawai." Duk abinda ta fad'a akan kunnuwansu, dan haka suka juya jiki a sanyaye suka fita daga gidan, cikin nutsuwa suke tafiya inda *Adamu* yace "Harira kina ganin idan muka je zasu sauraremu har su taimaka mana kuwa? Dan ni har yanzu a tsorace nake." Saida Harira ta share hawayen dake zubowa a idonta tace"Ban sani yah Adamu, iyayenmu sun cutar dasu sosai ta yanda ko basu yafe musu ba basu da laifi, matar yallab'ai Abbas kuma Sameera bana tunanin zata iya kallon fuskata ma, domin kuwa a lokacin da muke aiki a gidan na lak'a mata sharrin sata, kaga kuwa banda tabbacin zasu sauraremu." Rik'e k'ugu Adamu yayi suna tafiya a hankali yace "Wannan fanti da iyayenmu sukayi mana Allah kad'ai zai iya wanke mana shi, nifa yanzu duk da ina namiji har kunyar fita waje nake, har bana iya fad'in cewa ni d'an *Bukar* ne saboda abinda suka aikata." Da ire-iren wannan maganganun suka k'arasa tashar shiga mota, cikin sa'a suka sauka lafiya suka samu adaidaita suka lula unguwar zone 2, fadar Sameera aka ajesu inda mai gadi ya tambaye su "Wa ku ke nema?" Harira ce tace "Munzo ganin Sameera ne." "Me? Hajia kike kira haka gatsau?" Cewar mai gadin, Adamu ne yace "Kayi hak'uri yallab'ai, munzo ganin Hajia Sameera ne." K'asa da sama ya kallesu yace " Tasan da zuwanku ne?" Adamu ne yace "Gaskiya bata sani ba, amma ka taimaka mana mu ganta dan Allah, wallahi daga nesa muke." Saida ya sake kallonsu kafin yace "Ku bari na sanar mata tukun." Yana fad'a ya juya ya fito da wayarshi ya danna kira, a tabkekiyar kitchin d'in *Razeena* mai aiki ta ji kyakyawar wayar mai kama da masarrafin telebijin tayi k'ara, d'auka tayi tare da fad'in "Razeena ce akan layi." Mai gadin ne ya fad'a mata zuwansu Harirar tare da wanda suke son ganin, a cewarta "Zan fad'a ma Hajia yanzu." Aje wayar tayi kafin ta nufo falon Sameera, zaune ta sameta da *Ameer* (Mus'ab sunan mahaifinta) d'an shekara hud'u yana wasa saboda yau yan rigimar ne akanshi shiyasa ban je islamiyyar ba, sunkuyawa tayi tace "Hajia kinyi bak'i a waje, sunce ke suke son gani, su biyu ne mace da namiji, macen sunanta Harira sai namijin Adamu, sunce sun zo ne daga k'auyen gwagwa." Cike da jin dad'in yanda Razeena ta gama fahimtar halayyarta ta kalleta da mamaki, ta jima tana kallon fuskarta kamar tana son gano wani abu kafin ta zaro ido tace "Harira, k'auyen gwagwa?" Cikin ladabi tace "Eh madame." Tsaye ta mik'e ta kama hannun Ameer tace "Ki musu iso Razeena, na gane wace Harira." "Ok." Ta fad'a tana nufa k'ofar fita, ita ta bud'e musu k'aramar k'ofar suka shigo ta shigo da su, tana gaba suna biyarta suna k'arewa gidan kallo, Harira na tsananin mamaki wai Sameera ce a wannan gidan, wacce a lokacin da sukayi aiki ake mata kallo tsintacciya marar gata, saida ta shigo da su har falon anan Sameera dake tsaye har yanzu ta kalli Ameer tace " Ameer Kaje wajensu Ammie kuyi hira." Harari ta kalla tace "Ki kawo musu abun tab'awa." "To." Ta fad'a ta fice da shi, kallon Harira tayi wacce ta kafeta da ido tana kallo, sosai ta saki fuskarta d'auke da murmushi tace "Harira ku k'araso mana, ku shigo ku zauna." Saida taje ta kama hannunta ta zaunar da ita akan kujera inda shima Adamu ya zauna kamar akan wuta, kallon falon yake sai kace falon shugaban k'asa, a ranshi yace "Wasu na fafutukar neman abinda zasu ci, wasu kuma sun wadatu sunyi birgima a cikin kud'i, burinsu shine su tara dukiyar da har jikokinsu zasu mallaka." Muryar Sameera ce ta dawo dashi tana fad'in "Sannu ko, ya hanya?" Da "Lafiya lau." Suka amsa ta d'ora da "Harira dama kina nan? Ina kika shige haka ko labarinki babu?" Cikin sanyinjiki tace "Ina nan mana Hajia, ina k'auyen mu." Zaune Sameera tayi a kujerar data tashi tana fad'in "Amma shine kika b'uya kuma?" Murmushi kawai Harira tayi saboda fitowar wata mai aikin d'auke da faranti da kayan tab'awa da masu sanyi ta aje gabansu, saida ta zuba musu ta bawa kowa kafin ta juya zata tafi Sameera tace "Ku shirya mana wajen cin abinci saboda bak'i." Saida ta sunkuya tace "To Hajia." Ta fice, kallonsu Sameera tayi tace "Harira wannan mijinki ne?" Kallon Adamu tayi tace "A'a, yayana ne, uwar mu d'aya ubanmu d'aya." "Ayyah, Allah sarki, sannu ko." Ta sake fad'a tana kallonshi, da d'an murmushi ya amsa da "Barka Hajia, ya yara?" "Lafiya k'alau." Ta fad'a da murmushi sosai, maida kallonta tayi ga *Wassila* dake shirya kayan abinci a dinning duk da ba lokacin cin abinci bane, mik'ewa tayi ta kallesu tace "Bismillah Harira, ku zo ku ci abinci." Daga ita har Adamu babu wanda yace a'a saboda dama basuyi karin kumallo ba suka fito, k'arasawa sukayi suka zauna akan kujerun suna jinsu kamar akan wuta, suna kallo Wassila ta gama shirya komai ta zubawa kowa ta aje masa gabanshi kafin tace "Aci lafiya." Tana tafiya suka fara tsakurar abinci cikin kunya, Sameera kuma da dama ba ci za ta yi ba saboda ta ci abinci lemu kawai take sha, ganin suna kallon farantin dake gabanta yasa ta d'an fara kaiwa bakinta ita ma, ganin sun kasa sakewa yasa ta mik'e tace "Ina zuwa ko, ku ci dan Allah sosai, ku saki jikinku kamar gida kuke." Kicthen ta nufa inda suka bud'e sosai suka dinga cin abinci suna had'awa da naman ciki da lemu, saida sukaji cikinsu yayi k'at alamar ya cika kafin suka sarara suna kallon shi kanshi wajen cin abinci, sai lokacin Sameera ta fito tace su dawo falo, nan suka samu wuri suka zauna kafin Sameera tace "Harira, kince kun zo gani na ne, Allah yasa dai lafiya?" Saida Harira ta nisa sosai kafin tace "... *Kuna son ci gaban labarin ne ko kuwa???* *Barkanmu da sallah, Allah ya maimaita mana ya karb'i ibadunmu.* 27/05/2020 à 14:46 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💕 _*MASOYA NA*_💞 _Bismillahir rahamanir rahim_ _2_ "Sameera mun zo neman taimakonki ne, dan Allah ki taimaka mana kamar yanda Allah ya taimake ki, ki wa yallab'ai Abbas magana akan iyayenmu da ya sa baki a fito da su, wallahi muna cikin wani hali saboda rashinsu a kusa da mu." Shiru tayi tana goge hawaye kafin ta ci gaba da cewa "Sameera a dalilin abinda iyayenmu suka aikata yasa duk k'auyenmu an tsanemu, k'annan mu basa iya shiga cikin yara suyi karatu ko wasa ba tare da an tsagwamesu ba, haka muma dake manya a cikin hantararmu ake, ana fad'a mana an gadar mana bak'in hali, son kud'in iyayenmu yasa suke d'aure, Sameera in tak'aice miki wallahi aurena ya mutu saboda maganar iyayenmu nan, shi ya sa muka ce bara mu zo mu rok'i alfarma ko zaku iya taimaka su fito, izuwa yanzu nasan sunyi nadama tare da tuba akan zunubinsu." Cike da tausayi Sameera tace "Allah sarki, a gaskiya Harira na tausaya miki, amma meya shafi matsalar iyayenki da aurenki kuma?" Kallonta tayi tace "Sameera kinfi kowa sanin halin mutanen k'auye, abu k'ank'ane suke mayar dashi babba, da k'yar akayi aurena saboda kafewa da dangin mijina sukayi wai ba zai aureni ba, da k'yar akayi auren amma da nasan abinda zai faru a gidan aurena kenan da banyi auren ba ma, tun bayan aurenmu nake fuskantar matsi da takura a wajen iyayen mijina, ina hak'uri sosai wajen zama dasu tare da hak'urin da mijina ke bani, ko shekara bamuyi suka saka shi dole ya k'ara aure saboda cewa ban haihu ba, matsala ta sake rub'anya ne daga lokacin da amaryarshi ta zo, ita ma matarshi d'orawa tayi daga inda yan uwanshi suke min rashin mutunci, kullum habaici da k'ananan maganganu da zagin iyayena suke, a shekara d'aya ta haihu ni kuma shiru har lokacin, a haka na d'auki tsawon shekara hud'u ina wannan rayuwar har ranar da Allah ya kawo k'arshen zamana a gidan, kuma hakan ta faru ne sakamakon fad'an da mukayi da amaryarshi saboda ta zagi iyayena, nan ya goyi bayanta ya fad'a min magana sannan ya sake ni, kinji abinda ya faru Sameera, yanzu haka muna zaune tare da k'anwar mahaifiyarmu ce wacce mijinta ya rasu da kuma 'ya'yanta, wallahi ba zamu tab'a cewa muna jin dad'in zama da ita ba, saboda babu abinda take taimaka mana da shi duk da cewar tana sana'a." Kuka sosai take saida Sameera ta koma kan kujerar da take ta dinga rarrashinta, kallon Adamu tayi tace "Adamu kuyi hak'uri dan Allah, naji uzurinku kuma na tausaya muku sosai, amma ku sani ko Dadyn mamana (Abbas) bana jin yana da hurumin da zai iya fito da iyayenku, dalili kuwa shine an kamasu da laifin dumu-dumu kuma su da kansu sun amsa, hukunci ne aka yanke musu wanda dole sai su gama wa'adinsu, kunga kenan bana jin akwai taimakon da zamu iya yi muku akan maganar nan, yanzu hukuma ce ke da wannan hakk'in amma bamu ba, amma dan Allah kuyi hak'uri, amma a shirye nake da na muku wani taimakon idan kuna buk'ata." Adamu ne yace "Yanzu kenan babu abinda zaku iya yi mana?" Jinjina kai ta d'anyi tace "I think so." Kallon idonta yayi duk da haibar matar na mishi kwarjini amma haka ya daure yace "Amma idan kuka janye k'arar tare da yafe musu laifinsu ai ina ganin za'a sake su." D'an murmushin gefen labb'a tayi tace "Adamu kenan, magana ake fa akan wad'anda aka yankewa hukuncin." Ajiyar zuciya ya sauke yace "Kuma fa hakane, to yanzu meye abunyi dan Allah? Muna neman taimakonki Hajia, nasan idan kila saka baki zai iya yin wani abu akai." Dafa kafad'ar Harira ta kumayi tana kallonta tace "Harira ku nemi wani taimakon, amma maganar gaskiya Dadyn mamana ko maganar da zata tuno mishi da baya baya so anayi." Kallon kallo sukayi tsakaninsu kafin Harira tace "To in wannan ba zai samu ba Sameera ki taimaka min da ko shara ce ko wanke-wanken a gidan nan, ko na samu abinda zan dinga samarwa k'annan mu abinci." Adamu ne yace "A'a Harira, bake ke da wannan hakk'in ba, nine ya kamata na nemi aiki dan na ciyar da ku." Murmushi Sameera tayi tace "To ai ko dukanku kuka samu abinyi farin cikinku ne, dan haka wannan ba matsala bace Harira, in dai aikine kin samu a gidan nan ko da babu abinda zakiyi." Da farin ciki ta kalleta tace "Da gaske zaki d'auke ni aiki Sameera?" Ita ma dariya tayi tace "Me kuwa zai hana Harira, insha Allahu zaki fara aiki duk ranar da kika shirya." "To wane irin aiki zanyi? Dan naga akwai ma'aikata a gidan." Saida ta tashi daga kujerarta ta koma inda take ta kalleta tace "Um, gaskiya kam babu abinda babu wanda baya yinshi, amma idan zaki iya saiki zauna a b'angare na kina taimakawa ko da yara wajen shirin makarantar da kuma abinda ba za'a rasa ba." "Shikenan wai abinda zanyi?" Cewar Harira, murmushi kawai ta mata mai tsadar gaske, Adamu ne yace "Wannan ma da kika mana mun gode sosai Hajia, Allah ya saka da alkairi." "Ba komai." Ta fad'a a tak'aice, Harira ce tace "Yanzu yaushe zan fara aikin?" "Duk ranar da kike so Harira." Cewar Sameera, da azama tace "Ko gobe ma zan iya dawowa?" Dariya Sameera tayi tace "To da wannan me zai hana ki bari har jibi, lokacin munyi magana da Dadyn yara." "To shikenan, hakan ma yayi, Allah ya nuna mana jibi, mu zamu koma Hajia, mun gode sosai Allah ya saka da alkairi." Harira ta fad'a suna mik'ewa, itama mik'ewa tayi tace "Ina zuwa ko." D'akinta ta shiga kusan mintuna ta d'auka kafin daga bisani ta fito rik'e da leda babba a hannunta, tana zuwa ta mik'awa Harira tare da kud'i har dubu biyar tace su shiga mota, sai kuma Adamu data bawa kud'i shima har dubu arba'in tace "Ga wannan ka fara juyawa ko kafin muga yanda abubuwa zasu tafi." Har k'asa ya duk'a yana mata godiya ita kam kunya ce ma ta isheta saboda ya na gaba dasu, da haka suka juyo suka taho suna godiya sosai, tun a hanyarsu ta komawa Harira ta fara sak'awa zuciyarta wasu abubuwa na daban, tabbas ganin Sameera a wannan halin yasa ta ji tana hassadarta, abun takaici wai har su nemi alfarmarta ta kasa yi musu, wannan shine dalilinta na neman aiki gidan, saboda tana so ta cimma wani buri da yau ne ta kitsashi a zuciyarta, inda Adamu kuma yake ganin taimakon data musu ma yafi wanda sukaje nema mahimmanci, koba komai iyayensu sune masu laifi, laifinsu ya shafesu ta yanda shi kanshi harya rasa aikin lebarancin da yake ciyar da iyalinshi dashi, amma yanzu gashi ta bashi jarin da zai iya tsayawa da k'afar sa k'am, da wannan tunanin suka isa k'auyen su, tun a hanya suka rabu inda shi ya nufi gidanshi ita ma ta nufi gida. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Bayan tafiyar su da kamar minti ashiri *Bilkisu* ta shigo gidan tare da *Imranatu* dake d'auke da yaronta, kamar dai yanda suka saba kullum yanzu ma da sallama suka shigo Sameera ta amsa musu, kai tsaye Bilkisu kitchen ta nufa tana fad'in "Matar Abbas nasan dai ba kya rasa abin dad'i a gidanki, dan haka bara na samo abin tab'awa." Imranatu ce dake shirin zama ta aje yaronta tace "Ke dai wallahi anyi acici, ke ba kya da aiki sai ki kai bakinki." Tana kusa da shiga ta juyo tace "Lafiya ce ta kawo haka, da babu lafiya sai kun dinga lallab'a ta akan na ci." Dariya Sameera tayi tace "Gaskiya ta fad'a kuma, amma kuma abin mamakin bata tashi ciye-ciyenta sai ta zo nan gidan, bansan me ya sa ba?" Imranatu ce tace "Baki ji tace ba kya rasa kayan dad'i ba, ai da wannan ne kika rabamu da mazajenmu ta yanda basa iya cin abinci idan ba nan ba." Cike da murmushi tace "Kuma na samu kan mijina ba, kuma ai idan kuka so zaku iya rik'e su gidanku du dinga cin abinci." Hannu ta mik'awa yaron daya fara zagaya tsakiyar falon da rarrafe tace "Oya *Muhsin*, come on beby." Juyowa yayi cike da murna ya wangale baki ya taho da sauri, d'aukar shi tayi ta aza saman cinyarta ta ci gaba da hira da Imranatu, sai lokacin Bilkisu ta fito da k'aramin plate a hannunta d'aya hannun kuma da inibi tana sha, kamar jiran zamanta suke sai kuwa sallamar yara wasu da gudu wasu kuma a nutse, kasancewar yaran Imranatu dana Bilkisu duka tare suke karatu da yaran Sameera yasa gidan ya gauraye da hayaniya lokaci d'aya, gaishe da iyayen sukayi inda Raihan da kuma babbar 'yar Bilkisu *Fadila* da kuma 'yar Imranatu *Ma'awa* kasancewarsu yan wari ne yasa suka zaune akan kujerun suka fara cirewa k'annan su uniform, sai Abdul wanda har yanzu yake zuwa islamiyyar kafin hutunshi ya k'are, kallonshi sameera tayi da yayi zaune a kujera tace "Son an gaji ko? Ya karatun?" Cike da nuna kasala yace "Ammie karatu yayi zafi kam." A hankali cikin nutsuwa Raihan ta kalleshi inda Ma'awa ta amsa mishi da "Wallahi yah Abdul kai dai anyi rago, wai Ammie fa saboda yau ajinsu malaminsu bai zo ba shi aka wakilta a matsayin malamin shi ya sa yake fad'in haka." Kallonta yayi yace "Au, ke kin d'auka koyarwar sauk'i gareta? To gobe ki jaraba koyarwar ki gani." Bilkisu ce tace "Wannan ai ba zata iya ba, surutu zatayi ko karatu?" Turo baki tayi cikin shagwab'a tace "Mama." Kallonta tayi tace "K'arya na fad'a kenan?" Fadila da ke kallonsu kallon Abdul tayi cike da birgewa, cikin taushin murya tace "Yah Abdul ko zamu maka tausa ne?" Murmushin gefen labb'a ya mata yace "Nagode k'anwata, ba sai kin wahala ba." Cike da nutsuwa da sanyin jiki Raihan ta mik'e da kayan su *Diya'u* a hannu ta kalli Sameera tace "Ammie an gama abinci? Danni yunwa nake ji." Murmushi Sameera tayi tace "Kowane tsuntsu kukan gidansu yake, kowa da abinda ya dame shi, to kije ki watsa masu ruwa sai ku sauko ku ci abinci." Kama hannun Diya'u tayi tace "To Ammie kinsan fa yaron nan naki da iyayin tsiya wallahi kullum shi ke bani wahala wajen shirya shi." Diya'u ne ya fizge hannu yace "To Ammie ni nace bana so ko zan dinga yi wa kaina wankan, ai yanzu na iya amma sai ace wata ce zata min." Da kallo Sameera ta bishi kafin ta girgiza kai tace "Ki rabu da shi kawai tunda ya girma zai iya da kanshi." Ba zato ba tsammani sukaji Ameer ya fashe da kuka, Sameera na waigawa taga shi da Khlifa ne, shiru tayi sai Raihan ce ta isa garesu ta shiga tsakani ta tambayi meya faru, Ameer ne ya fara fad'in abinda ya faru inda Khalifa yace "Ammie wato dan yana mai sunan Baba ne na daka shiyasa kikayi shiru." Abdul ne ya kama hannun Khalifa yana fad'in "In banda abinka bros ai dukanku kun sanya mana uwa a tsakiya ne, kai Abban ta ne (mahaifin Abbas) shima kuma Ameer abban ta ne (mahaifinta), to yanzu a fad'an nan wa kake so ta shigarwa?" Cike da wayo yaron yace "Ni mana, tunda ni surukine, kaga akwai kunya tsakaninmu." Zasu wuce ne ta gaban Sameera ta daki mazaunanshi tace "Ya dai yau naga *aku na* ba karsashi haka?" Kallonta yayi ya turo baki yace "Ammie kema parrot zaki kirani dashi kamar yanda tsofaffin can suke fad'a." Janyo shi tayi ta rumgume a k'irjin ta tace "Ayya! Sorry Dady na, ba haka nake nufi ba, na ga dai ka shigo ba magana ne." *Raudat* ce ta fashe da dariya tace "Ammie yunwa yake ji fa shiyasa." Hararan Raudat tayi tace "Ba fa nasan sharri kinji, Abba na k'arko ne da shi yunwa ba zata sa shi ya zama rago haka ba." A kasalance ya kalli Sameera ya shafa cikinshi yace "Ammie yanzu dai bara na haura sama na sauko, idan na ci abinci zaki sha labari." Bushewa akayi da dariya sai Raihan da ita dai murmushi ne nata dan sam yarinyar bata da hayaniya kuma bata son hargagi a rayuwarta, komai cikin nutsuwa da sanyi take yin shi. Sama suka nufa haka ma Abdul da Jabir, Imranatu ce ta fito da makullin gida ta bawa Ma'awa tace "Kije ku canza kaya ku ci abinci, ki kula da kyau kar a hargitsa min lissafin gida bayan na gama gyara komai." Sameera ce ta kalli yaran dake fita ta kalli su Imranatu tace "Jiya munyi magana da Abban Raihan akan maganar Abdul da Raihan d'in, yace yana tunanin yi musu baiko idan mun dawo daga bikin *Arfat* (yar kawu *Bakura* yaya ga iyayensu Sameera da Abbas), yace idan so samu ne yana so a d'aura musu aure saiya tafi da matarshi idan hutunshi ya k'ar." Bilkisu ce tace "Kuma hakan ba wata matsala? Ni har yanzu gani nake Raihan yarinya ce wallahi." Sameera ce tace "Ba wata matsala yar uwa, tunda dai ta balaga ta kai matakin da zata iya d'aukar namiji ai shikenan, zamu kiratada yarinya ne idan bata zama mace ba, amma kinga Raihan bana da shakku a kanta, na yarda da ita ta yanda zan iya kaita gidan mai mace biyu ma saboda nasan na bata horon da zata iya zama da kowa." Bilkisu ce tace "Kuma gaskiya kika fad'a, to amma ya waccen maganar?" Saida Sameera ta sake kallon yaran dake ta ficewa har yanzu sai Fadila data rage ita ma tana shirin fita tace "Maganar gwajin jinin da za'a mishi wannan ba matsala bane, tun farko ma yallab'ai ya b'ata lokaci ne saboda ganin rashin dacewar hakan." Imranatu ce tace "Banga laifinshi ba gaskiya, haka kuma banga laifin su Ammie ba, amma haka zai daure yasan abunyi dan lokaci k'uracewa yake, yanzu ana fara maganar zasu ce ina sakamakon yake, amma kinga idan aka tabbatar da lafiyarshi ai mu kan mu hankalinmu a kwance yake, tunda wannan cutar ta *HIV* ana d'aukar ta, kuma akan iya haihuwar yaro da ita ma idan ba Allah ne ya kareshi ba." Bilkisu ce tace "Oh Allah ka nuna mana wannan rana, ranar da alk'awarin nan zai cika na auren Raihan da Abdul." Murmushi Imranatu tayi tace "Ameen ya Allah, Allah yasa muna cikin masu rai da lafiya." Cak Fadila ta tsaya daga shirin fitar da take daga d'akin, sakin jakar hannunta tayi ta fad'i k'asa saboda jin wani abu ya daki zuciyarta da k'arfin gaske, kasa motsawa tayi daga wajen kamar wacce aka d'aure, take kuma hawaye suka cika mata ido har suna zarya a kumatunta, muryar Bilkisu ce ta katseta da cewa "Wai tsayuwar me kika wa mutane anan kuma? Kinsan dai *Farisa* (k'anwar ta) ba zata iya bud'e gidan ba ko." Rintse ido tayi wasu hawaye masu zafi suka sake antayo mata, a hankali ta bud'e tare da had'e wani k'ululun abu da taji ya tokare mata mak'oshi, sunkuyawa tayi ta d'auki jakarta ta wuce ba tare da tasan ina take saka k'afar ta ba, tabbas yarinya ce ita kuma mai k'ananan shekar, sai dai tasan tana matuk'ar jin Abdul a zuciyarta fiye da yanda take jin komai, tana ji a duniya inhar za ta yi aure to Abdul ne zata aura, ta yarda wannan so d'in da suke jin ana labarinshi ya kamata, ta kuma tabbatar a yau d'in nan taji wani tafasashen kishi ya taso mata akanshi, da haka suka isa nasu gidajen wanda dama had'e suke waje d'aya, kamar yanda iyayen suka d'ora su akan turbar kula da k'annan su yanzu ma haka ce ta kasance, duka yan matan uku kowace ta taimakawa yan uwanta k'anana wajen yin wanka da canza kaya, saidai Fadila bata tare da walwala sam, haka ta shirya musu sahu sukayi sallah tana wannan halin, dan ko dinning ma da suka zauna cin abinci ita bata ci ba, ta dai zauna saboda kar ta gusa yaran suyi wata b'annar, saida suka gama taga sun mik'e zasu fita tasan ina kuma zasu je, saida ta je har k'ofar gidan taga shigarsu gidan kawun nasu (Abbas) kafin ta rufe gidan ta haura sama izuwa d'akin ta, tana shiga ta fad'a kan gado ta fashe da kuka dan shine kad'ai taji tana buk'atar tayi, ita kanta bata san ya akayi ba kuma yaushe ta fara son Abdul, ta dai san kawai yana birgeta tun farko har lokacin da take jin wasu abubuwa a game da shi d'in. Ma'awa ce ta had'u da su Farisa ta tambaye su ina Fadila, Farisa ce tace "Tana gida bata fito ba." Juya akalarta tayi ta nufi gidan, dan ya zama kamar ibada a wajensu tarewa gidansu Raihan a kowane lokaci su da iyayensu, ta jima tana bubbuga k'ofar falon amma shiru bata bud'e ba dan bata ma san tanayi ba saboda tana saman bene, haka ta gaji ta dawo gidan sai dai bata ji a ranta cewa wani abu ne ke faruwa ba, dan haka ma bata damu kanta ba, ko da ta shiga gidan kai tsaye wajen su Ammie ta nufa, kamar yanda ta sani kam ta same su duka a falon na su anata hira, inda Abba ya fito farfajiya tare da duka yara mazan, sai Khalifa dake rik'e da hannun Abban yana ta zuba mishi surutu, hakan ne yasa ya juyo ya kalleshi yace "Ka dubi Allah ka k'yale ni da zancen islamiyyarku nan, wai kai d'aukar rahoto ne ke kai ka makarantar? Saifa na je na fad'a wa malaman na ku su killace ka kai kad'ai tunda lek'en asiri ke kaika makarantar ba karatu ba." *Usman* (mai sunan kakansu Abbas baba Ard'o) ne yace "Abba shi fa labari ne bai iya bayarwa ba, sai yace komai daya faru saiya fad'a." Juyowa Khalifa yayi ya harare shi yace "To ina ruwanka, na sa da kai ne a maganata?" Take ya mayar da kallonshi ga Abba yace "Kana ji ko aboki na, sai yaron ya..." Dakatar dashi Abba yayi jin zai ci gaba da bayar da labarinshi yace "Kunga wa zai min karatun da aka koyar da shi yau d'in nan na bashi kyauta?" Da sauri Khalifa ya d'aga hannu sama yace "Ni ne, zanyi." "To fara ina jinka." Cewar Abba, saida suka zauna a gardine akan kujeru sannan Khalifa ya fara rera kuratunshi tun farkon suratul *Mulk*, murmushi kawai Abba keyi saboda farin ciki, zai iya cewa suruntu da wayon yaron ne yasa yake da matuk'ar k'ok'ari ko a school ko islamiyya, saida ya kai k'arshe sannan ya tsaya yace a bashi kyautarshi, dole Abba ya bashi kyautarshi kad'ai ya rabu da shi. *ZARIA* *K'auyen Dabai* *Salma* ce ta fito daga ban d'aki rik'e da buta a hannunta sai d'aya hannun dake rik'e da sandar dake taimaka mata wajen tafiya, da k'yar ta k'araso ta zauna akan tabarmar dake k'ofar d'akin ta, sai dai kuma wata masifaffiyar yunwa take ji wacce ke neman kaita gushewarta, dan har ta manta rabon data samu abinci mai kyau ta ci, tunda mahaifinta ya rasu tsananin rayuwarta a k'ara bunk'asa, dama kuma matar mahaifin nata ba k'aunar ta take ba, hasalima tana da hannu sosai a shigarta duniya, dan ita ce ta shanye mahaifinta ta yanda baya iya ja da maganarta, matsi da takura kuma suka sakata barin gidan gaba d'aya, yanzu kuma gashi daga ita sai matar baban nata a gidan, amma ba zama take ba tunda mahaifinta ya rasu ta had'a gonarshi ta siyar da kuma rabin gidan da suke ciki wai ta tafi neman kud'i, yanzu haka duk in tana son cin abinci saidai tayi bara ta samu abinci wanda hakan yana k'ona mata rai sosai, *Ma'aruf* da *Ma'arufa* kam dama bata ma kwance da su, dan in suka fita tare sai suyi wata d'aya basu zo k'auyen ba da sunan ganinta, kuka ta fara wanda ya zamar mata jiki tare da nadamar abubuwan data aikata a rayuwarta, ta jima tana kuka kamar ranta zai fita kafin ta ji yunwa na takurata sosai, da k'yar ta ciccib'a ta tashi tsaye ta d'auki wani tsohon hijabi ta saka ta fita daga gidan. Duk inda taga gungun maza nan take tsayawa tayi bara, amma ba kowa ke bata ba saboda da dama mutanen k'auyen sun tsaneta, wasu kuma k'yank'yami ne na ganin tana saurin kai hannunta tana susar gabanta dake mata bala'in k'yaik'ayi har yanzu, da k'yar ta samu naira 60 ta siye garin kwaki harna talatin da kuma sugar na goma, canji ta k'ulle a zane saboda kuma gaba, haka ta sake rarrafowa ta nufo hanyar gida zuciyarta ba dad'i ko kad'an, tunanin halin da take ciki da kuma rayuwar da 'ya'yanta suka d'aukarwa kansu wacce bata da maraba da irin rayuwar da tayi. *Bayan fitarta* da wasu mintina Ma'arufa da Ma'aruf suka shigo gidan, masha Allah yaran fa an girma sosai, sai dai kana ganinsu ba zaka ce Salma ce ta haifesu ba, dan kuwa sam basa kama da ita, ga mai da ma'arufa ke shafawa wanda yasa tayi jawur har tana d'aukar ido, kallon gidan suke kamar yau suka fara shigowa kafin Ma'aruf ya shiga d'akin yana fad'in "Wannan gurguwar banzar ko ina ta tafi kuma?" Ma'arufa ce tace "Waya sani, watak'ila ta tafi yawon barar data saba." Tsaki yayi yace "Bara na yi wanka na koma inda na fito, wallahi ba dan ke kika matsa ba ni da ban zo k'auyen nan ba." Shiru ta masa sai shiga d'akin da ita ma tayi, duk da ta same shi yana cire kayanshi hakan bai dameta ba, aje jakarta tayi akan katifar da bata da maraba da tabarma, cire d'an kwalinta tayi ta zuge zip d'in rigarta ta cire, haka ya rage mata daga ita sai bras da pant ba tare da jin kunyar yayanta ba, d'an kwalinta ta d'auka ta warware ta juya baya ta cire bras ta d'aure k'irjin ta da kallabin, zage pant d'in ta tayi sannan ta juyo zata fita daga d'akin, idonta ne suka sauka kan ma'aruf daya saki baki yana kallonta yana had'iyar yawu, sosai yaji sha'awar yar uwarshi na ratsa shi ta ko ina, dama zaman da suke a gidan masu zaman kansu d'aki d'aya suke, haka yana yawan faruwa tsakaninsu ba wani abu bane su a wajensu, basa damuwa dan sunga tsiraicin junansu, sai dai wani abu bai tab'a shiga tsakaninsu ba, kowa harkar gabanshi yake da na shi mutanen, amma kuma duk da haka shed'an yana tusa musu sha'awar junansu, ita kanta Ma'arufa tana irin hakane saboda tana so ta d'auki hankalinshi ya nemeta, shi kuma yana so ya nemeta amma yana jin rashin dacewar abun a zuciyarshi. Fitowa tayi ta duba duk inda tasan zata samu ruwa amma babu, tsaki tayi ta lek'a d'akin tace mi shi "Dan Allah ka fito ka samo mana ruwa waje gidan nan babu ruwa." "Babu ruwa ne?" Ya fad'a yana cire belt d'in shi, banza ta masa ta fito ta zauna akan turmi, fitowa yayi da riga a hannu yana shirin sakawa yace "Ina zan samo ruwa yanzu a wannan busashen k'auyen?" Wajen ban d'aki ya nufa ya d'auki bokiti ya juyo da nufin fita idonshi suka sauka kan Ma'arufa, k'aramin d'an kwalin data d'aura k'irji dashi yasa duk cinyarta a fili suke, ba wai cinya kad'ai ba har gabanta yake hangowa daga nan, ganin yanda yake kallon k'asan ta yasa ta sake ware k'afafun ta tana kashe masa ido, aje bokitin yayi ya nufi wajenta da azama, yana zuwa durk'ushewa yayi gabanta yana kallonta ido jawur cikin wata irin murya mai d'aukar hankali ta bariki yace "K'anwa... ta zaki iya...amincewa da..ni?" D'aga hannayenta tayi tana wata irin mik'a mai tafiya da ruhi ta cije leb'en ta na k'asa, hannunshi ya d'ora a cinyarta yana shafa d'aya hannun kuma saiya fara tafiya dashi a hankali harya sauke shi a gabanta, yatsanshi yasa ya dinga wasa da gabanta wanda yasa ta fara narke masa harta had'a bakinta da na shi, mik'ewa sukayi daga nan suna rumgume da juna ba tare da sun raba bakin su ba, suna daf da shiga d'aki suka ji muryar Salma tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Ma'aruf!" *Allah ka karemu ka kare mana zuri'armu, Allah ka shirya mu ka shirya mana zuri'armu, ka gafarta mana zunubanmu.* 27/05/2020 à 16:35 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWU NA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ _3_ Zaune tayi kamar kayan wanki tana fad'in "Ma'aruf abinda kukeyi kenan dama? Ashe dama kusancinku bana shak'uwa bane na iskanci ne, amma ko Allah ya wadaranku wallahi, bak'in cikin da kuke saka min Allah ya saka muku ninkin baninkin shi, tsinannu kawai la'anannun Allah, kai yanzu inba tab'ewa ba duk matan duniya ka rasa wacce zaka nema sai k'anwar ka da kuka fiti ciki d'aya, tir da halinku shegu kawai..." Ma'arufa ce ta kasteta da fad'in "A'a dakata haka malama, ya isa kinji ko, addu'ar ki ba zata sani jin haushi ba domin kuwa ke Allah ya fara tsinewa kafin mu, dan haka ai ba wani abun kunya bane, hakan ma shine zai tabbatar da mun gada kenan ga uwa ga uba, sannan naji dad'in sunan da kika kiramu da shi na shegu, wannan shine asalin sunanmu dama, amma daga yau karki k'ara mana katsalandan a rayuwarmu kamar yanda a lokacin da muke yara muna kallonki kina rayuwarki babu wanda ya saka miki ido, ina fatan kin fahimta." Juyawa tayi ta shiga d'akin Salma na fad'in "Dan ubanki ai ni duk iskanci na banyi da wanda yake d'an uwana ba, har nayi yawon bariki na gama ban tab'a nema da wanda ya sanni ko na sanshi ba, amma kuma fa? Ciki d'aya fa kuka fito, ni ce nan na haifeku." Ma'aruf ne ya tab'e baki yayi yace "And so what dan ke kika haife mu, naga dai abun kunya ba kanmu ne aka fara ba bare ace zai k'are a kanmu, ke tab'argazar da kikayi ma waye zaiyi irinta a duniyar nan, shine har zaki wani mana fad'a sai kace hallitarmu ki kayi." K'wafa yayi yana shirin shiga d'akin ta dakata da kukanta tace "Amma ai duk iskanci na ni ban tab'a iskanci da wanda ke d'an uwana ba ko da na nesa ne bare kuma shak'ik'i, kawai ku dai ku ce taku tsinuwarce tafi tawa." "To sai me? Idan har mu tsinannu ne ke fa? ke da kike cin amanar mijinki da amininshi, kika haifi yara har biyu a gidanshi da sunan nashi yaran dan kawai ki ci gadonshi, yanzu ba gashi nan ba wa gari ya waya? Ba kud'in, ba farin ciki, ba jin dad'i." Salma kam kallon Ma'arufa kawai take dake fad'a mata magana son ranta, Ma'aruf ne ya d'ora da "Kula ba k'afa ba, sannan duk fitsararmu bamu tab'a neman jinsinmu ba, amma ke fa? Kinyi tarayya da 'yan uwanki mata ma saboda lalacewa, a haka har zaki mana wani wa'azi." Cikin kuka ta dafe k'irji tace "Ina uwarku kuke fad'a min duk abinda ya zo bakinku? Wallahi kunyi asara." Ma'arufa ce tace "Hum! Wannan kuma ke ta shafa." Ma'aruf ne yace "Kwad'ayi ai mabud'in wahala ne dama, yanzu gashi baki samu komai ba sai wahala da kike, abinda zaki ci ma gagararki yake yi, shi kuma Abbas yana can da matarshi da yaransu cikin farin ciki sun ma manta da wata hallita wai ita Salma kamar dai yanda suka manta da wannan rub'abb'en margayi Abban." Cikin jin haushi da takaicin ambatar sunan Sameera tace "Amma ai har yanzu Abbas bai sake ni ba, tunda abinda ya faru ya faru bamu sake had'a ido ba, dan haka ni nasan bai sake ni ba har yanzu." Wata dariya Ma'arufa tayi tace "Kaji matar nan da hauka, to tsufanki ne ke nuna miki har yanzu ke matarshi ce? Domin Allah ke yanzu ko mata sun k'are a duniya me zaiyi da ke." Ma'aruf ne yace "Inhar gaske ne ma bai sake ki ba to ina inada tabbacin bai sake ki bane saboda yana so sai kun had'u ido da ido, dan nasan sakin da zai miki sai ya kai dubu biyar." Dariya suka dinga yi mata har Ma'aruf ya saka rigarshi ya nufi k'ofar fita, ta gaban Salma ya bi inda take zaune k'ofar shigowar saboda abinda ta riska, ledar garin kwakwinta da sugar ya kalla yace "Gurguwa gari zaki sha? Bari idan na fita zan siyo miki kifi ki d'an ci dan nasan anjima ba'a had'u da abu mai lami ba." Ma'aruf data zauna kan turmi ce tace "To ina za ta ga abu mai lamin, ai ta gama cinye nata rabon tun gidan waccen mutumin." Ko da ya fita Salma ta yunk'ura da sandarta ta zauna kan tabarmarta, kallon Ma'arufa tayi tace "D'auko min kofi da cokali a d'aki." Shiru Ma'arufa tayi kamar ba taji ta ba har saida tayi niyya ta mik'e ta d'auko mata, kawo mata tayi daga tsaye ta jefo kofin ta koma ta zauna, nan ta gyara kwakin tana ci tana kallon Ma'arufa cike da takaicin wayar da take jin tana yi da saurayi wacce batsa tafi yawa, saida tayi maganin yunwar dake damunta kad'ai nutsuwarta ta dawo jikinta, a hankali maganganun yaranta suka dinga dawo mata, sai kawai taji bata buk'atar tsayawa da yak'in daga nan, gashi tun ranar da *Tahir* ya harbe mata k'afa ta gama jinya ta dawo k'auyen nan bata sake ganin Abbas ba, tasan ba zai iya ci gaba da zama da ita ba, sai dai kuma bata san a wane matsayi take ba tunda bakinshi da bakinta bai had'u ba har yanzu, ga kuma tunanin Sameera wacce ta raina amma yanzu ta tabbatar ita ce sarauniyar gidan Abbas kuma sarauniyar zuciyarshi, da wannan tunanin ta riski wunin ranar, har saida zuciyarta ta sake durmiyata kan wani zunubin kuma, sai dai wannan karan ba ita za ta yi fad'an ba, tunda tana da yara kamar Ma'aruf da Ma'arufa, tana da yak'inin cewa su Abbas ba zasu iya shaida su ba tunda sun girma duk sun canza daga yanda suka san su, sai bayan magriba Ma'aruf ya shigo gidan da ledoji a hannu. D'aya leda ya mik'awa Salma yace "Alk'awarin dana miki ne, ki ci kema kiji dad'i." Sauran ledar kuma kujera yar tsugunno ya janyo ya zauna gaban Ma'arufa ya bud'e yace su ci, kallonshi Salma tayi ta kalli ledar taga gasassar zabuwa ce da kuma balangu, sai lemu mai sanyi guda biyu alamar dai shi da ita, aje ledarta tayi gefe d'aya tana kallonsu suna ci tace "Ku saurare ni da kyau muyi magana." Ma'aruf ne kad'ai ya iya ma kallonta kuma take ya ci gaba da cin abincinshi, cikin d'aga murya tace "Da ku fa nake magana kuna jina ku min banza." Ma'arufa ce tace "To wai ba kunne ne ke ji ba, ki fad'a mana amma ki tabbatar serious magana zaki fad'a." "Akan Abbas ne." Ta fad'a tana kallonsu dukansu, kallonta sukayi suka ce "Kamar ya Abbas, meye faru?" Ba alamar wasa tare da ita tace "Ku yanzu kuna son ku k'arar da rayuwarku a haka kamar ni? Ni a wahalce ku a wahalce, abincin ma sai nayi bara na samu ke kuma sai kin sayar da matancinki, kuna ganin wannan ita ce rayuwar daya kamata mu ci gaba da yi? Ku tuna fa kuna yara irin gata da soyayyar da Abbas ya nuna muku, amma haka ya rabu da ku yanzu gashi kuna cikin wahala, shin ba kwa jin kuna son kuyi wani abu a game da haka?" "Kamar me fa?" Cewar Ma'aruf kafin ya d'ora da "Duniya na da tabbacin mu ba 'ya'yansa bane bare mu ce muna da gadonshi, ke baki kyautata masa ba bare muce zai kallemu da mutumci ko dan zaman tare da akayi, duk da dai mutum ne mai son taimako musamman matasa, amma bana jin zai iya taimakonmu saboda abinda kika masa." Kallonsu tayi da shu'umin murmushi tace "In tambayeku mana? Shin ya zakuji ace yau kun wayi gari kun samu million ashirin ashirin naku na kanku?" Ma'arufa ce ta saki wata k'ara tace "Wooo! Ai wallahi Hajia kud'in nan suka shigo zaki sha mamakin irin rayuwar da zanyi." Ma'aruf kam cewa "Ai gurguwa wannan kud'in suna zuwa ni da zama nigeria kuma sai dai in nayi sha'awa kawai insa a nuna min ita ta babban majigin allon kallona dake mak'ale a gadona na alfarma." Cike da makirci Salma tace "Dan haka kuwa zaku samu wannan kud'in cikin sauk'i inhar kukayi abinda zan fad'a muku yanzun nan, ku zaku huta, ni ma kuma zan huta." Ai da sauri suka gyara zama suna fuskantarta suka ce "Muna jinki Hajia." Dalla dalla Salma ta musu na abinda take son su aiwatar duk da kuwa had'arin shi da kuma muninshi, su kuma dayake magana ce ta kud'i sam basu duba komai ba musamman Ma'arufa wacce ita ce zata fi shiga had'ari tare da rasa wani abu na ta, amma a wajen su wannan ba damuwa bane idan da kud'i, saida ta gama kitsa musu Ma'aruf ya bushe da dariya yace "Kai gurguwar nan har yanzu ashe kanki da sauran wuta, ai shirin nan yayi d'ari bisa d'ari wallahi." Ma'arufa ce ta wani girgiza gaba har saida k'irjin ta suka motsa tace "Alaji yaka ganni gaban *oga Samuel* da millon ashirin a account d'ina? Kaga a ranar zan samu 'yancina kuma zai zama kawar bawa na." "Gaskiya kam, duba kiga yau kafin ya barmu mu taho shege kamar wani ubanmu, harda jaddada mana yake kar mu wuce gobe." Salma ce tace "Waye kuma Samuel? Kwartonki ne ko?" Cikin nuna rashin damuwa tace "Um um, wanda muke zaune a gidan shi ne, tunda ya bud'a ido ya ga nice hasken gidanshi ni ke kawo mi shi manyan costumer yake nanik'e min, baya so ina nisa dashi ko nan da can, kuma dama lokacin da muka je gidan ba kud'in d'aki ne damu ba, shiyasa saiya bamu d'aki a cewa shekara zan biya shi, duk da yanzu yasan ina tare da mutanen da zasu iya biya min kud'in, amma baya so na bar gidan ne shiyasa baya karb'ar kud'in har yanzu, kuma yayi hakane saboda wanda suke zuwa gurina suna masa alfarma sosai a siyasance, a ikonce da kuma arzik'ance, sannan ga kyautar da suke mishi ta fitar hankali." Tab'e baki Salma tayi tace "Inhar kukayi abinda nace to ba Samuel ba, har wad'anda ke neman naki zaki iya had'a kafad'a da su." Ma'aruf ne yace "Ai ki kwantar da hankalinki, kamar anyi angama ne, goben nan muna komawa zamu fara shirye shiryen komai yanda ya dace." "Da kyau." Cewar Salma tana murmushi, haka sukayi kwanan farin ciki da tunanin samun kud'i kamar wanda suka bayar ajiya, haka gari ya waye bayan Ma'aruf ya samo musu abin kari sun gama suka shirya komawa inda suka fito, abun mamaki saiga Ma'arufa ta dunk'ulo har dubu uku ta bawa Salma ta rik'e kafin su sake dawowa, Ma'aruf kuma ya bata k'aramar wayarshi saboda su dinga kirantatana sanin abinda ke faruwa cikin gaggawa, haka suka d'auki hanyar komawa zaria kafin su wuce abuja. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Zaune yake a farfajiyar gida akan kujera yayi shiru sai dai idonshi jawur suke da wani hoto a hannunshi yana kallo, ba zai iya tantace abinda yake ji ba a game da wacce ke cikin hoton, sai dai ko ba komai yasan har yanzu yana matuk'ar sonta, amma abinda ta mishi na k'ona masa rai sosai, haka kuma wata zuciya na tuna mishi da cewa ba laifin ta bane, laifin ta d'aya shine b'oye mishi da tayi harta aureshi da cikin wani a jikinta, yana wannan halin ne k'annan shi dake bi mishi ya shigo gidan kuma kai tsaye wajen ya nufa, tsaye yayi yana kallonshi ganin hawaye na neman zubo mishi yasa yayi gyaran murya, da sauri *Abbacar* ya kalleshi tare da sanya hoton aljihun gaban rigarshi yana k'ak'aro murmushi yace " *Saleem* kai ne? Yaushe ka shigo? Ai banji shigowarka ba." Murmushi yayi ya rumgume hannayen shi yace "To dama ina zaka ji bayan *Zeenat* ta tafi da gaba d'aya nutsuwaka." Murmushi ya sake yi da bai kai ciki ba yace "Hmmm." Sunkuyawa yayi ya dafa cinyarshi yace "Yaya Abbacar wai sai yaushe wannan tunanin zai k'are ne? Baka tunanin kana shiga hakk'in iyalinka dayawa? Yanzu da ace *Sayyada* ce ta fito ta sameka da hoton tsohuwar matarka wacce ta cutar da kai ta ruguza mana farin cikinmu tayi d'aid'ai da rayuwarka, me kake tsammanin zata ji a ranta?" Murmushi dai ya sakeyi yace "Hoton Zeenat ne fa ba ita d'in ba, kuma ita kanta Sayyada ai tasan da ina kallon hoton ina kuma tuna baya." Cikin kulawa Saleem yace "Yaya Abbacar, na fahimci har yanzu kana son Zeenat a zuciyarka, amma kuma kana jin zafin abinda ta aikata maka ko?" Girgiza kai yayi yace "Ko d'aya Saleem, kawai dai ina tuna rayuwar baya ne." Murmushi rainin hankali yayi yace "Karka raina min wayo mana yaya, nasan abinda kake ji a ranka mana inhar zan kwatantashi da kaina." Kawar da kai yayi yace "Ko kad'an Saleem babu haka a raina, sai ma addu'a da nake binta da ita Allah ya mata rahama." Tsaye ya mik'e yana kallonshi yace "Kenan kana so ka ce sam baka jin zafin cin amanar da Zeenat ta maka? Kenan ko ka tuna cewa aminin yayanta ne ya lalata ta sannan ya mata ciki wanda ta zo da shi gidanka baka jin komai?" Tapi ya dinga yi yana dariya yana fad'in "Amma gaskiya kayi k'ok'ari yaya, kaga kuwa idan da ni ne haka ta faru dani da tuni zuciyata ta buga, dan ni ba zan iya zaunawa a duniyar nan ba ina tunanin matar da ta shigo da cikin wani k'ato gida na ba, to taya ma haka zata faru? Matata ta sunna na haskota a ido na tare..." " Stop it Saleem, ya isa." A hankali Saleem ya kalli yayanshi da tuni hawayen nan dake mak'alewa suka fito, rufr idonshi yayi zuciyarshi na bugawa da k'arfi yana ji kamar ya mangare Saleem d'in, a hankali ya bud'e ido ya sauke a kanshi ba tare da yace komai ba ya mik'e daga kujerar, kasancewar har yanzu yana da yar matsala wajen tafiya saboda tun lokacin da yayi paralysé yasa bai iya tafiya da kyau, cikin jan k'afa d'aya ya shiga cikin falo ya bar Saleem nan, da kallo ya bishi harya b'ace kafin ya rik'e k'ugu, har k'asan zuciyarshi yana jin zafin ganin d'an uwanshi a wannan halin, halin da ba kowa yayi sanadiyar shigarshi ba sai mace, tabbas Zeenat ta cutar da su sosai, domin kuwa a dalilinta ne har yanzu yayanshi baya iya tafiya daidai, a sanadin abinda ya faru dashi ne yasa mahaifiyarsu data rage musu kwantawa jinya wacce dama take tare da hawan jini, suna ji suna gani ta mutu da bak'in cikin abinda Zeenat d'in ta musu, yanzu gashi shi kanshi Abbacar d'in baya da aiki sai tunanin ta da zubar da hawaye, shi kad'ai ne yake gani yaji dad'i tunda babban magajin nasu yana Gombe acan yake harkokinshi tare da iyalinshi, sai in ya zo duba su kawai ko kuma su sunje. D'auke hannayenshi yayi d'aga k'ugu yana d'an cije leb'e da wani irin yanayi a tare da shi mai wuyar fassarawa, ko cikin gidan bai shiga ba ya sake shiga motar shi ya bar gidan, duk da dai yasan Abbas shima kuma ya sanshi, amma hakan ba shine zaisa ya fasa abinda yayi niyya ba, domin kuwa duk da abinda ya faru sam su Abbas basu raba alak'arsu da Zeenat ba, ko ba komai dai yar kawunshi ce wacce ita ma ta taka muhimmiyar rawa a rayuwar shi. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Da dare suna zaune dukansu kamar yanda suka saba kullum bayan sun gama cin abinci, hira suke sosai ana dariya sai dai yaran tsakaninsu suke hira haka ma manyan, ana haka Sameta ta kalli Abbas da suka fi kusa tace "Sir, ina da magana fa da kai." Ameer dake ta mak'ale mishi a wuya yana ci gaba da wasa da shi yace "Ina jinki, amma kafin nan sau dubu nawa na fad'a mi ki bana son sunan nan?" Turo baki tayi tace "To ai idan na fad'i sunan ne saina dinga tunawa da baya, lokacin da bana iya kallon idonka kullum kaina k'asa ina fad'a, good morning sir, good evening sir, sir your food is ready, sorry..." Bata k'arasa ba ya dakatar da ita yace "Heee, ya isa to naji, fad'a min abinda zaki fad'a min, idan ba haka ba zaki sa Ammie ta ji kina tuna baya yanzu zata fara mita akan bautar da ke da akayi a baya." Dariya tayi tace "Kai kuma shine baka so ko a tuna baya? Saboda kasan baka da gaskiya." Saida ya sumbaci bakin Ameer yace "Indai ba fad'a kike so muyi ba a daren nan to ki fad'i abinda zaki fad'a." Tab'e baki tayi tace "Tunda na tuna baya kuma ai kaima kasan dole muyi fad'a, dan kasani dai ba tsoro nake ji ba." Sai lokacin ya kalli k'wayar idonta cikin k'ara k'asa da murya yace "Na gano ki munafuka kawai, wato neman hanyar fad'a kike dan na biye miki muyi bala'i a daren nan, dan kinsan a k'arshe kowa zai kwana d'akin shi ne ko kuma ki kawo mana Ameer a tsakiyarmu ko, to ba zanyi hushi ba kuma ba zanyi masifar ba can kiji da abarki." Tashin su Naseer da iyalensu ne yasa suka kallesu Abbas na fad'in "Ya dai malamai naga kun mik'e?" Bashir ne yace "Yaya wallahi bacci muke ji, zamu je mu kwanta ne saida safenku." Hararanshi yayi yace "Ku d'in ne zaku kwanta tunun yanzu?" Wani kallo Sameera ta masa tace "Yallab'ai, miji da matarshi yace bacci yake ji, meye na ka a ciki dan Allah?" Bilkisu ce tace "Yafi so muyi ta zama anan ke kuma saboda gobe da ace ya makara bai tashi ba yace surutun mu ne ya hanashi bacci." Kallonta yayi yace "To ba surutun naku ke hanani baccin ba? Musamman ke da wannan mai..." Ya fad'a yana nuna Sameera wacce ta tilasta mishi yin shiru saboda kallon data masa, fuska a had'e tace "Ka k'arasa mana kai nake sauraro." "Shikenan kawai abar maganar." Ya fad'a yana sunkuyar da kai, mayar da kallonta tayi garesu sukayi ban kwana kusan duka yaran saida suka zo suka bata hannu suna fad'in saida safe, su Abba ma tashi sukayi suka musu saida safe, Abbas ne cikin shafar kai ya mik'e ya tari gaban Ammie da Ameer yace "Ammie na ce ko zaku tafi da Ameer wajenku ne yau dai kam ya tayaki hira har kiyi bacci." Wani kallo ta masa tace "Ban gane ba? Ni na fad'a maka ina son ya tayani baccin? Me zaisa ba zai kwana tare da yan uwanshi ba kamar kullum?" "Eh to Ammie, da yake wai naga kamar baku tashi bacci bane yanzu." Yana fad'in hakane dan yasan Ameer da rigima zai iya cewa a wajensu zai kwana, ko kuma idan suka samu sab'ani da uwarshi tace anan zai kwana tare da su, shi kuma yau kam yanda yake jinshi babu abinda zai hanashi sukuwa idan har ya samu filin nan. Kallon Ameer tayi wanda keta latsar wayar Abbas bai ko san sunayi ba tace " Wannan sarkin had'iyar ne zan tafi dashi ya kwana wuri na, ai kafin gari ya waye duk ya cinye min katakon dake d'aki na." Su Raudat da suma suke shirin tashi ne suka bushe da dariya, sai Raihan da murmushi kawai tayi wanda ya bayyanar da hak'oranta, Abba ne ya kamo hannu Ameer d'in yana fad'in "Yanzu takwaran nawa ne kike fad'a ma wannan maganar? Lallai ma matar nan kin samu wuri dayawa, aboki muje d'aki na ka kwana kaji ko." Abbas ne yace "Kuma fa Abba madarar ma da yake tashi yasha cikin dare yanzu ya daina, tunda yayi yawu kunga ai baya zauna wuri d'aya ba." Ammie ce ta tab'e baki tace "Ai ina d'aga mishi k'afa ne ma saboda yana da sunan na ka, amma badan haka ba ai daya gane kurenshi." Kamar daga sama Khalifa yace "Wai ke da duka mazanki sai kinyi fad'a ne? To idan kika b'ata mana dukanmu ya zakiyi kenan?" Da yatsa Ammie ta nuna shi tace "Kai rufe min baki a wurin nan, ina shirin bacci ne zaka sani cacar baki, kai idan za'a kwana a hantse ba gajiya zakayi ba, parrot kawai." Hararan ta Khalifa yayi yace "Zan kama ki ne tsohuwa." Nuna Abbas tayi tace "Kaga tsohon nan bani ba." Kallonta Abbas yayi yace "Ammie maganar mata ce fa, ai da Ammienshi kika kira tsohuwar ko." Wani kallo ta masa tace "Kai yanzu waccen ta maka kama da tsohuwa a ganinka? Ko dai ba kya duban madubi ne?" Abba ne yace "Kai kuwa ina zata kira 'yar gwal da tsohuwa, ai sai kai data raina kuma da bata haifa ba, amma ai abin a fili yake kowa yasan waye tsoho a cikinku." Sun jima tsaye wuri d'aya suna wannan gardamar da cacar bakin kafin kowa ya nufi makwancinshi, da k'yar Abbas ya karb'i wayarshi a hannun Ameer wanda yace da ita zai tafi ya kwana, saida Sameera ta shirya cikin kayan bacci ta nufi fita dan zuwa d'akin Abbas, a k'ofa suka had'u wanda ya kasa jira yake ganin kamar ba zata zo ba, yana shigowa ya rufe d'akin ya rage hasken wutar d'akin, rumgume juna sukayi a cikin kunne ya rad'a mata "Kinsan da nayi kewarki?" "Uhmmm." Ta fad'a cikin mak'oshi, cikin salo ta fara tsotsar bakinshi har tayi nasarar kama harshenshi, salon da take masa yasa ya fara jin kamar bashi ba, ana cikin haka ta raba bakinsu ta zura harshenta a kunnenshi ta fara wasa da shi a ciki, wata sanyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da k'ara k'amk'ameta, daga nan komai ya canza abun ya girmama zuwa kan gado. *Bayan awa biyu* dukansu bacci ne ke son d'aukar su, cikin taushin murya Abbas yace "My Meera ina son haihuwa dayawa har cikin zuciyata, shin kina ganin nan gaba zaki iya haifo min yara shida? Kinga idan aka had'a da wanda muke da sai su zama goma sha biyu cif." Zunbur ta tashi zaune tana kallonshi tace "Da gaske kake yallab'ai? Amma fa ni na d'auka zamu barsu ne daga guda shidan, kaga nima na huta ai." Lumshe ido yayi ba tare daya tashi zaune ba yace "Wallahi iya gaskiyata nake fad'a miki, ina so naga kin haifa min yara dayawa, amma idan ba zaki iya ba saina..." Kafeshi tayi da ido tace "Sai kayi me? Ka k'ara aure kake nufi?" Bud'e ido yayi a kanta yace "Eh mana, tunda ke ba zaki iya ba." Gyara zama tayi ta d'auki pillow ta soma dukanshi dashi tana fad'in "Je kayi auren dan Allah ga wurin nan, wallahi kana aure zan koma basraba da zama, ba zan k'ara saka kaina a had'ari ba saboda kai tunda kuskurenka ne." Da k'yar yayi sa'ar rik'o ta ya had'a da jikinshi sosai ya sake lumshe ido yana murmushi, ita kam k'ok'arin raba jikinta da nashi take amma ya matseta sosai, masifa take tana fad'in "Rabu dani malam ka tashi ka koma d'akin ka, 'ya'yan ne ba zan haifa ba kaje kayi auren, naga ma ko Salma ai zaka iya dawowa da ita ta haifa maka yaran tunda har yanzu baka saketa ba, humm, wallahi kana bani mamaki mutumin nan, na ce ka saketa ka ce kayi tun tuni, na tambayeka saki nawa ka mata amma ka gagara fad'a min, nasan ma baka saketa ba saboda kana sonta har yanzu, watak'ila ma kana zagayawa wajenta ban sa..." Da k'arfi ya matseta sosai ya danna bakinta a nashi yana mata wata mahaukaciyar tsutsa, shiru tayi tana saurarenshi saida ya saketa da kanshi kafin ya kalleta da idonshi kamar zaiyi bacci yace "Mai sunan mamana surutunki ya fiki yawa, idan kika fara bala'i ba kya tsayawa ko numfashi ki sauke." Zata yunk'ura ta tashi ya sake matseta yana shafa gashinta yana fad'in "Shiiiii, yi bacci kinji ko, yi baccin abinka." Kamar zatayi kuka tace "Amma fa na fad'a maka tun tuni cewa zamuyi magana." Cikin magagin baccin dake fizgarshi yace "Ki bari da safe zamuyi maganar kinji." "Maganar fa na da mahimmanci." Shiru ya mata baice komai ba hakan kuma yasa ta tashi zaune tace "Uhum wato ba ma ka da lokacina ko, to gaskiya ban yarda ba tashi muyi maganar, dan idan nace sai gobe to wuri ya k'ure." Yanda take jijjigashi ne yasa ya bud'e ido ya sauka daga kan gadon ya nunata da yatsa yace " Allah badan ina tsoron hushin Ammie ba dana tsula miki d'an karan duka a daren nan, wai Sameta yaushe ne zakiyi hankali ke? Har abada ace ba zaki bar mijinki ya huta ba kamar wata..." Bai k'arasa ba ya juya ya bar d'akin, dan dama maganganun daya fad'a mata ya fad'a ne dan karta bishi d'akin shi saboda ya santa da zuciya, shiyasa ya tak'aita daga nan, yana shiga d'akin shi ya kwanta amma saiya kasa bacci, dan basa raba shinfid'a inba rigima sukayi ba ko sunyi fad'a, tunanin halin da take yanzu yakeyi kafin daga bisani ya fara tunanin Salma, tabbas ya saki Salma tun ma ranar daya gane da sihiri ya aureta, sai dai bai fad'a ma kowa ba inba Abba ba, amma da ana saki billion daya ma salma, da wannan tunanin bacci ya d'auke shi. Sameera ma haushin maganganun daya fad'a mata ne suka sakata yin kwanciyarta tana huci, ta kuma san safiya nayi zai fara bata hak'uri yana cewa dan ta barshi yayi bacci ne ya fad'a mata hakanan, da haka ita ma bacci ya d'auke ta. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Tunda Harira ta koma gida ta samu Baaba mai wake ta fad'a mata ta samu aiki a gidan tsohon mai gidanta, bud'ar bakin Baaba cewa tayi "Karki raina min hankali mana Harira, wane irin aiki ne mutanen nan zasu baki bayan abinda ya faru? Kawai ki fad'i gaskiya idan karuwanci zaki fara, koda yake ma ba wannan ne karo na farko da zaki fara ba, amma ki sani wallahi ni babu ruwana duk abinda kika je kikayi can ke kika jiyo da matsalarki." Bata damu da abinda ta fad'a ba haka ta ci gaba da shirye shiryen tafiya, da dare kuma ta tara k'annan ta a d'akin su ta fad'a musu zatayi tafiya, Karime ce mai wayon cikinsu dan haka tafisu shiga damuwa, sosai Harira ta rarrasheta tare da nuna mata zata je yin aiki ne dan su dinga samun abinci suna ci suna k'oshi, sannan ta dinga biya musu kud'in makaranta akan lokaci, sannan ta cire dubu uku ta basu a kud'in da Sameera ta bata tace ta b'oye karta yarda Baaba ta gani, haka kuwa akayi haka suka kwana da tunanin wayewar garin gobe. *Mu had'e a shafi na gaba insha Allah.* 29/05/2020 à 11:10 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 *Wannan kyautar taku ce* _My Heenat_ _My BK_ _Aunty Aishan Umma_ _Mamienmu_ _Maman Annur (ma chérie)_ _Momyn Dady_ _My Hawwa_ _Sweet Hawwer_ _Sis Chappa_ _Mamar Hassan_ _Yar Baba (yar tsohuwa😜)_ _Rahila_ _Voisine Ruky_ _Auntynmu *Madame Dakoro*, jinjinar ban girma tare da fatan alkairi zuwa gareki, hak'ik'a samun masoyiya kamarki abun alfahari ne ga kowane mutum mai zuciya, alkairi yana da dad'i komai k'ank'antarshi, farin cikin da kika saka *habibiyata* yasa naga ya dace nima na mik'o godiyata zuwa gareki , domin kuwa duk wanda zai farantawa wani na kusa da kai, to hak'ik'a kai ya farantawa, da wannan nake miki addu'a Allah ya sama rayuwarki albarka, Allah ya jik'an mahaifa, Allah ya albarkaci rayuwar 'ya'yanki, Allah ya k'ara yalwata miki, Allah ya k'ara dank'on soyayya tsakaninki da mijinki, Allah ya saka miki da gidan aljanna, wannan k'ok'ari da kike Allah ne kad'ai zai iya biyanki, fatan farin ciki *mdm Dakoro*._👍 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _4_ *Tunda safe* Abbas ya shirya saboda tafiyar data kama shi dolenshi zuwa k'asar *Belgium*, a wannan lokacin yasan Sameera na kitchen dan in har yana gari da kanta take had'a mishi abin break, dan haka ya kira da téléphone d'in dake kitchen d'in, tafi kusa da wayar dan haka Razeena na matsowa zata d'auka ta kalleta tace "Bari na duba." Tana d'orawa a kunne tace "Hello." Murmushi ya saki kamar tana gabanshi yace "Uwar gida sarautar mata, daga kanki an gama mulki na kowane fanni, matar Abbas kuma k'anwar Abbas sannan garkuwar Abbas, uwar 'ya'yan Abbas kuma wacce ke mulki a zuciyar Abbas, farin cikin gidana, na ce ko zan iya ganinki a part d'ina yanzun nan?" Duk da kalamanshi sun bala'in fasa kanta kuma taji dad'i sosai har zuciyarta, amma dayake daren jiya ya b'ata mata rai sai ta dake tace " Why not? I'm coming." Saida ya sake kashe murya yace "Takawarki lafiya 'yar sarki jikar sarki k'anwa ga sarki mai mulkin garin *Basraba*." Aje wayar kawai tayi kafin ta kalli Razeena tace "Ki kula da sauran aikin, ina zuwa yanzun." K'ofar falon tasa makullinta ta bud'e ta shiga, wani katafaren falo ne daya gaji da kyau da tsaruwa, duk da tayi mamakin ganinshi zaune akan kujera yana d'aura takalminshi k'afa ciki bak'ak'e sai shek'i suke da d'aukar ido amma saita sake had'e rai ta rumgume hannaye tana kallonshi, d'ago kai yayi ya kalleta har dariya na kusan kubce mishi, amma dariyar da zaiyi itama rigima ce zai b'allowa kanshi dan haka yayi shiru, har ya gama d'aure takalmin ya mik'e tsaye yana ci gaba da kallonta ya kuma d'auki jakarshi bak'a ya d'ora a kafad'a, tabbas yayi kyau ya kuma birgeta, dan gaba d'aya bak'ak'en suit d'in daya saka sun zabge mishi shekarunshi, gabanta ya tako ya tsaya yana kallonta yace "Are you stil angry with me?" Kai ta d'aga mishi alamar Eh, dan haka ya kamo hannunta ya marairaice yace "Sorry mai sunan mama na, tafiya zanyi yanzu bana so na tafi kina hushi dani, please kiyi hak'uri ki manta kinji." Wani kallo ta masa ta zage hannayenta tace "Abban Raihan wai me ya sa yanzu kake min haka? Sam yanzu baka da lokaci na, jiya fa magana na ce zanyi da kai amma ka k'i ban dama, amma yanzu ka tsaya gabana kana fad'a min wai zakayi tafiya." K'asa yayi da kanshi yayi shiru saboda baida hujjar kare kanshi, ya sani shi kanshi yanzu ya zama buzy sosai, ba kuma komai ya janyo hakan ba sai gabatowar zab'e, duk da baya siyasa amma yana da ruwa da tsaki a harkar sosai ta yanda ya kan zama haka, kallonta yayi yace "Amma ai nace kiyi hak'uri ko." Cikin hassala tace "Amma ai hak'urin jiya ne ka bani, kuma ban hak'ura ba har sai ka fad'a min me ka so fad'a a k'arshen zancen ka." "Na fa riga da na sha maganin zama dake Meera, kin daina wahalar dani yanzu." Shine abinda ya fad'a cikin ranshi, amma a fili saiya shagwab'e yace "Dan Allah ki yafe min, tafiya zanyi fa na fad'a miki, kinsan kuma ance tafiyar hali, ba lallai na dawo garekkkk..." Bata bari ya k'arasa ba ta rufe mishi baki da tafin hannu tace "Shiiii, please don't say that, you know i love u, huh?" K'asa tayi da kanta sharrr sai hawaye saboda duk lokacin da yayi maganar rabuwa ko mutuwa to ta kan tuna had'arin daya shiga a baya ne, rumgumeta yayi yana shafa bayanta yace "I love u too my Falmata." Sun jima haka yana rarrashinta kafin yace "Yanzu fad'a min me kike son fad'a min tun jiya?" Kallonshi tayi tace "Na so fad'a maka tun jiya a lokacin da kake cikin nutsuwa, yanzu kuma gashi zakayi tafiya bana so mu samu mis-understand ka tafi kuma kana hushi dani." Shafa kumatunta yayi yace "I promise u ba zan fahimceki ba daidai ba, so teld me what's going on?" Saida ta d'an ja baya ta zauna kan kujera kafin ta nuna mishi kusa da ita tace "Please have a sit." Zaunawa yayi yana kallonta yana fahimtar yanda maganar ke mata nauyin fad'a, sai dai baisan kome take son fad'a ba haka, dan shi dai abune mai wuya ganinta irin wannan yanayi, babu wani abu da take jin tsoro ko shayin fad'a masa sai dai in bai zo bakinta ba ko tunaninta, da k'yar ta had'a ido da shi kamar marar gaskiya tace "Dama jiya ne, Harira ta zo...nan.tare da yayanta, sun zo neman taimakonka akan iyayensu da ke rufe a cell , n...na...na fad'a musu hakan ba zai yiwu ba., shine sai ta nemi wani taimakon nawa..., kuma nayi mata." Wani kallo ya mata kamar mai son gano wani abu kafin yace "Idan na fahimceki daidai kamar Harira tsohuwar mai aiki kike magana a kai ko?" A hankali ta d'aga mishi kai alamar Eh, d'auke kallonshi yayi aga kanta yana kallon gefe, ya jima haka kafin ya kalleta yace "Wane irin taimako kika mata?" Ganin yanda yake kallon ta yasa gabanta fad'uwa tare da jin tsoron fad'a mishi, shirun da tayi yasa yace "Na ce wane irin taimako kika mata?" Nan ma shiru tayi sai k'yabta ido da take, wani kallo ya sake watso mata yace "Are you a deep?" Girgiza kai tayi da sauri alamar a'a, dan haka yace "To fad'a min." Cikin sark'ewar murya tace "À...a..aiki Na...bata..., a gi...ggg.idan.nan." Da k'arfi ya mik'e harda buga kujerar yace "What nonsence? What traying to teld me? Harira? A gidana? Harira again." Mik'ewa tayi ta kalleshi tace "You promise me." Juya baya yayi ya rik'e k'ugu yana sauke numfashi, ya riga daya mata alk'awari, sannan akwai alk'awura da dama daya mata wanda burinshi kullum ganin ya cika mata su, daga ciki kuwa harda mallaka mata gidan nan da duk abinda ke cikinshi, dan haka ya daidaita nutsuwarshi ya juyo gareta yace "Kina ganin hakan ba matsala?" "Insha Allahu ba za'a samu matsala ba." Kallonta ya sakeyi yace "Are you sure?" Cike da tabbatarwa tace "I'm very sure." "Kin yarda tayi aiki a gidanki?" Nan ma cewa tayi "Na amince da hakan, ina ganin kamar mun taimaka mata dan suna buk'atar taimako, kuma kaga yanzu bazawara ce ita ba budurwa ba, ta k'ara hankali da rayuwa da kuma nutsuwa." Ya so nuna mata illar yin hakan, amma yanzu yana kan hanya ne dan haka ya rik'o hannaunta d'aya yana murzawa yace "Falmata." K'ura mishi ido tayi dan inhar taji ya kirata da sunan Falmata to tabbas abinda zai fad'a yana da mahimmanci kuma iya gaskiyarshi ne zai fad'a, d'orawa yayi da "Sanin kanki ne na miki alk'awari da dama wanda a kullum nake son ganin na cikasu, sannan gidan nan na jima da mallaka miki shi ya zama naki har abada, dan haka banda ikon hanaki yin abinda kike so, ki kawo Harira gidan nan amma da sharad'i d'aya." Zaro ido tayi tace "What, sharad'i kuma?" Murmushi yayi yace "Yeah, da me kike tunani?" "To ina ji fad'a min." Ba alamar wasa yace "Sharad'in shine ko da wasa bana son ganinta a part d'ina bare naga k'afar ta a falon nan, ko da kuwa me ake ko kuma me ke faruwa ko zai faru, kin amince?" Murmushin jin dad'i tayi tace "Sauk'i kamar shan ruwa, dama ba wannan aikin zatayi ba, dan haka i agreed." D'aga kafad'a yayi yace "Then, all the best wifey." Rumgumeshi tayi sosai harda kukan shagwab'a tace "Zanyi kewarka mijina." Shima saida ya sauke ajiyar zuciya yace "Ba zaki tausaya min ba ni halin da zan shiga babu rigimarki a kusa da ni." Ba tare data d'ago ba tace "Oho, kenan ma ni d'in rigimammiya ce ko?" Matseta yayi yace "Number one ma kuwa in this world." Da k'yar suka rabu baya ya mata alk'awarin zai dawo nan da kwana uku da ikon ubangiji kad'ai ta barshi ya tafi, saida suka fito falo sun samu yara na zaune suna jiran break, sai Raihan da ita ma ake had'a break d'in da ita, gaisheda mahaifin nasu sukayi kafin ya fad'a musu zaiyi tafiya, addu'a suka bishi da ita kafin kowa ya fad'i abinda yake so a siyo mishi musamman ma Ameer da Abdul raheem, daga nan kuma part d'in su Ammie suka wuce dan basu riga sun shigo ba, nan ma addu'a yasha kafin ya wuce cikin rakiyar Sameera har zuwa bakin motarshi, drivenshi ne ya bud'e mishi amma saida suka k'ara rumgume juna kamar karsu rabu kafin ya shiga mota driver ya jasu, cikin minti talatin suka isa filin jirgi inda suka samu *captain Ali* ya gama shirya komai shi kawai yake jira, nan ma driver ya bud'e mishi ya fito yabi bayanshi da jakarshi, wata budurwa ce tsaye a k'ofar matakalar jirgin cikin uniforme d'in ta tana ganinshi ta d'an sunkuyar da kanta ta gaishe shi, ko kallon fuskarta baiyi ba ya amsa da "Fine." Yana fara takawa ita ma ta karb'i jakarshi a hannun driver ta bi bayanshi, suna shiga ciki matakalar ta d'ago ta rufe a hankali, jirgin dai gashi babba amma cikin inda yake zaune duka kujerun guda hud'u ne, biyu b'angaren dama biyu na hagu suna kallon juna, captain Ali ne ya fara sanar dasu jirgi zai tashi su kimtsa tare da daidaitawa, ba b'ata lokaci jirgin ya haura sama suka fara tafiya, wannan budurwar ce ta fito ta tambayeshi ko da wani abu da yake buk'ata, a tak'aice kawai ya fad'a mata da favorite d'in shi yake so, ba jimawa ta kawo mishi wata fresh milk kalar kad'ai abar kallo ce, haka suka dinga tafiya inda wannan matar duk minti talatin takan zo ta tambayeshi da abinda ya ke so, cikin yardar ubangiji sai ga k'afafun su sun taka k'asa bayan kwashe musu su da akayi, nan ma airport d'in wata motar ce ta d'auke shi zuwa wata babbar hotel ta manyan mutane. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Ko da su Ma'arufa suka sauka gidan masu zaman kansu kai tsaye d'akinta ta bud'a ta shiga, inda Ma'aruf ya shiga nashi d'akin shi ma, kaya ta cire ta fito ta d'ibi ruwa ta shiga wanka babu wanda ta kula duk da habaicin da wasu daga cikin mutanen gidan ke mata, Ma'aruf kuma fitowa yayi ya tsaya akan wasu dake buga karta a kan tabarma yana kallonsu, tana fitowa Ma'aruf shi ma ya shiga ba jimawa ya fito, amma kai tsaye d'akin Ma'arufa ya shiga hakan kuma ya haifar da k'ananan maganganu a wurin, dama dai tun zuwansu gidan basu fad'i alak'ar dake tsakaninsu ba cewa su yan uwane, sai dai wasu sunfi zargin dadiro kawai suke kuma suna rainawa wasu hankali suna karb'ar kud'in wasu mazan, yana shiga ya sameta tana saka bras, bayanta ya tsaya tare da kama hannayenta kamar zai saka mata sai kuma ya b'alle mata, a hankali yake shafa harya zura hannayenshi ya cabko nonuwanta ya masu wata matsa, cike da barikance tace "Ahhhhhh, huhhhhh." Juyowa tayi ido a lumshe tasa hannu ta kamo gabanshi tana lasar leb'e tace "Dama ina da haushinka, tsohuwar gurguwar nan ce ta kawo mana cikas." Zata had'e bakinsu ya juyar da kanshi ya kai bakinshi a kunnenta yace "Yau kuma zan huce wannan haushin nawa, dama wannan na jima da haushinsu." Cikin rashin sanin ciwon kai da rashin kunya da fitsara da rashin albarka suka dinga iskancinsu kai kace mata da miji ne, daga ita har shi ihu kawai suke sun mata a cikin mutane suke, suna cikin wannan bad'alar tasu wayar Ma'arufa ta fara ringing, amma saita zura hannu ta kashe wayar tana ci gaba da ihu, cike da bushewar zuciya take fad'in "Ahhhhh, washhhhh, D'an uwa na, huhhhhhh, wallahi duk kafi min kolayan banzan nan, ashe haka kake dama hhhhhhh, ahhhhhhhh, wayyo, harder." *Allah ka shirya mana zuri'a* Sallamar wani daga cikin masu neman Marfu'a ne wanda yake kira ta k'i d'agawa ta katse musu hanzari, tsaye yayi yana muzurai ya kalli wanda ke karta yace "Marfu'a ta zo ne?" Wani d'an daudu ne ya kalleshi ya yatsina fuska cikin harshenshi na mata yace "Kaga wani sabon salo kuma shafa kwalli da tab'arya, to yanzu duk nan cikin mu wa ka aje ya maka gdinta da zaka mana tsaye haka saman ka kana tambayarmu ita." Wani jan kallo ya masa zaiyi magana wata mace tace "Ka wuce mana tana ciki, mu ka tsaremu ka tambayemu ita kamar ajiyarta ka bamu." Su Marfu'a dake d'aki suna jin ance ya wuce ta zabura ta mik'e dan ita tasan masifar *Labo*, da sauri ta kalli Ma'aruf tace "Labo ne fa, yi sauri shiga nan." Ta nuna mishi bayan wasu tarin kaya, ba musu kuwa ya tattara rigarshi da wando ya kutsa ciki yayi shiru, saida ya kalli takalmin dake k'ofar d'akin na Ma'aruf kafin ya wuce ciki ko sallama babu, shigarshi kuma yayi daidai da Ma'arufa dake kwance kan gado tana gyara d'aurin k'irjin ta, wani kallon tuhuma ya dinga bin d'akin dashi harda ma ita kanta, da k'yar ya tsaya gabanta ya yaye zanin jikinta, ganin babu komai jikinta yasa yace " Me hakan ke nufi? Ke da wani d'an iskan ne a d'akin?" Kamar zatayi kuka tace "Wai me yasa kake hakane Labo, ni da wa ka gani a d'akin nan? Zuwa na fa kenan daga k'auye wanka kad'ai nayi." "To amma takalmin uban waye na gani a k'ofar d'akin, tunda dai ba naki bane." Kamar wacce ta tashi daga bacci tace "Uhum! Ina jin takalmin Big (Ma'aruf suke kira da haka a gidan)ne, ina jin ma harya fita ai." Jin ta fad'i haka yasa ya kalleta ya sunkuyo tare da kwantawa gefenta, hararan gefen ido ta masa tana yak'e, shi kuma nan ya fara shafarta yana fad'in yayi kewarta, na d'aya idan ta hanashi samun abinda yake so bala'i zai fara yanzu watak'ila ya had'a da dukanta ma , na biyu kuma tana buk'atar kud'i shi kuma tasan a wannan fannin indararo ne baisan ciwon kud'i ba, dan haka tana ji tana gani ya sake mata wawiyar caccaka. Ma'aruf na cikin kaya yana jin duk tsiyar dake faruwa yayi luf abin shi, sun jima kafin ya saka kayanshi ya fito da kud'i ya jefo mata ya fice, d'aukar kud'in tayi ta kalli k'ofar daya fita tace "K'aramin d'an iska kawai, kaji da bak'in halinka." Juyawa tayi inda Ma'aruf ke k'umshe ta bushe da dariya tace " Big sai a fito ko tunda dodon ya tafi." Fitowa kam yayi daga cikin kayan yayi sharkaf da zufa yana kallonta yace "Yarinyar nan ba ki da mutumci wallahi, ina cikin d'akin kuma shine zaki yarda ki biyewa waccen bunsurun." Tsaki yayi ya juya zai fita tace "To kuma aikin daka fara fa?" Juyowa yayi ya kalleta yace "Allah ya kiyaye na jefa gugata bayan Labo ya cire tashi gugar, sai kuma wani lokacin yarinya." Juyawa yayi yaji tayi tsaki ta kuma cewa "D'an iska kawai, kawai ka ce ba zaka iya ba." Saida yasa takalminshi ya kalleta yace "Ke wai jakar ina ce d ba kya gajiya? Yanzu duk abinda ya faru kice baki gaji ba." Mik'ewa tayi tsaye ta rarumo zani ta d'aura a k'irji tace "Haihuwar Salma ce fa, ko ka manta ne, gadon juriya nayi." Wucewa yayi zai shiga d'akin da yake kwantawa mutan gidan suka saka shewa da habaici wai suna nuna ba komai amma kuma da wani abu a k'asa, d'an daudun nan kad'ai ya kalla ya malmala mishi wata ashar ya wuce ya barshi. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Bayan tafiyar Abbas Sameera ta samu Ammie lokacin Abba shima ya fita, nan ta fad'a mata abinda ke faruwa yar aikin data d'auka, Ammie ce ta kalleta da mamaki tace "Takwarata, kuma ke yanzu kin yarda ki taimaka mata? A gaskiya ni dai hankali na bai kwanta ba." Cikin rarrashi tace "Ammie, wallahi babu abinda zai faru da yardar Allah, kuma ma Ammie ai ba su suka aikata laifin ba, kinga ba zamu hukuntasu da laifin da iyayensu ne suka aikata ba." Ajiyar zuciya ta sauke ta kalleta tace "Shi ya amince ne?" Da fara'a tace "Ammie munyi magana da shi kuma ya amince, kawai yace dai bai yarda taje ko kusa da d'akin shi bane bare kuma ciki." "To shikenan, Allah ya taimaka mana." Saida ta kwanta kan k'afafun ta tace "Ameen Ammie na." Shafa bayanta ta fara yi tana fad'in "Ya kamata fa kisan girma kikeyi takwarata, shiyasa kullum mijinki ke k'orafin ni na lalataki kika raina shi." Sake gyara kwanciya tayi tace "To Ammie idan banyi ba wa zan ma, shekaru na d'auka babu soyayyar uwa a tare dani saita uba, shiyasa ma ban damu da Abba ba kamar yanda na damu dake, Ammie nayi rayuwar kad'aici da maraici wanda har yanzu idan na tuno na kanji ba dad'i, soyayyar uba goma d'aya take data mahaifiya k'waya d'aya tak." Hannu Ammie tasa ta juyo da fuskarta tuni hawaye sun fara mata zuba, goge mata yake tana fad'in "Nasan da haka takwarata, shiyasa ma har yanzu bana kallonki a matsayin wata babba, nasan kinyi kewar mahaifiya a kusa dake, kin rayu cikin mutanen da baki da wata alak'a ta jini dasu, amma yanzu ba gashi komai ya wuce ba kina tare da ni." Rumgume Ammie tayi sosai kamar tana bata nono, tana jin soyayyarta na sake shiga zuciyarta, sai dai har yanzu tana ji ina ma zata ga mahaifiyarta ido da ido ko na awa d'aya, da zata k'arar da lokacin wajen nuna mata irin yanda take son rayuwa da ita. Sallamar su Raihan ce tasa ta tashi zaije tana kallonsu cikin kayan makarantarsu, Ameer ne ya taho da gudu ya fad'a da jikinta yana kuka wai shi ba zai je makaranta, kallonshi tayi tace "Haba dai Babana, da girmanka da komai ka ce ba zaka je makaranta ba, dubi fa kowa ya shirya kuma tafiya zasuyi , kamata yayi ace kaine ma shugaban tafiyar nan, ko ba kaso ka zama kamar Abba ne?" Cikin kukan ya amsa da "Ina so." Murmushi ta masa tace "Good man kenan, dan haka ka wuce gaba ka rigasu shiga gaban mota, kaji ko." Aida gudu ya juya ya bar d'akin, sai lokacin ta kalli Abdul da suke gaisawa da Ammie, suna had'a ido yayi k'asa tana gaisheta, amsawa tayi tare da cewa "Har kun gama shirin kenan?" Da alkunya ya amsa da "Mun gama Ammie, amma kuma bamu ga Dady ba." Murmushi tayi tace "Sai dai kuyi hak'uri kam, amma yanzu haka dadynku na sararin samaniya akan hanyarshi ta zuwa Belgium." Raihan ce tace "Ammie Belgium fa, amma shine ko ya mana sallama." Raudat ce tace "Ai zai dawo gidan ya samemu, Allah ba zan mishi magana ba." Sameera ce tace "To sarauniyar masu wayon duk duniya, kuna bacci ya tafi, amma bai fita daga gidan ba saida yace na tabbatar na sumbaci dukanku a madadin shi." Khalifa sarkin surutu da sauri ya fad'o jikinta yace "Ni ne farkon da za'a farawa, dama ko a haihuwa nine farin cikinshi na farko." Tab'e baki Raihan tayi tace "Dallah malam matsa min daga nan, taya zaka zama farin cikinshi na farko bayan an haifeni kafin kai." Matsowa tayi kusan Sameera ta sunkuya tace "Ammie ni ce farko." Hararansu Sameera tayi tace "Ga Abdul babban amma saiku da kuka fi kowa son girma." Hannun Abdul ta kamo ta matso dashi kusanta, kunya ce ta rufe shi dan shi yanzu kallon suruka yake mata ba uwa kad'ai ba, haka ko ta dafe kumatunshi ta sumbata tare da shafa kanshi tace "Allah ya albarkace ku yarana." Cike da jin dad'in addu'ar ta yace "Ameen Ammie, mun gode da addu'ar ki gare mu." Jabeer ta kamo shima ta masa kafin Raihan da Khalifa da kuma sauran yaran, bye bye suka musu suka tafi har Khalifa na juyowa ya kalli Ammie yace "Yar tsohuwa naga sai kallona kikr yau ban kulaki ba ko, to zan siyo miki goro idan zan dawo." Tab'e baki tayi tace "Ka ci k'aniyarka ko da kai da goron." 🤴🏻 *Masautar Basraba*🤴🏻 Sarki Imran Musayyib ne zaune akan sofa wacce tasha kwalliya mai d'aukar ido da birgewa, sanye yake cikin kaya na alfarma kuma na sarauta, sai dai babu nad'i a kanshi sai hula kawai, hatta takalmin k'afar shi irin na sarauta ne masu kwalliya daga sama kuma rufaffe, sai gefenshi liman ne tare waziri suna kallonshi da girmamawa yace " Liman kunce zakuyi magana dani mai mahimmanci, shiyasa ma na ce mu zo nan ciki saimu tattauna." Duk da yana sarkinsu amma suna jin dad'in yanda yake girmamasu saboda shekarunsu da kuma dad'ewarsu a fada, dan tun mahaifin Sameera na kan mulki suke tare da su har mahaifinshi ya karb'a kuma shi yanzu gashi a kai, liman ne ya kalli waziri yace "Waziri sai kayi bayani ko." Kallonshi waziri yayi ya kuma kalli sarki yace "Ranka shi dad'e Allah yaja zamaninka, dama magana ce data shafeka ta kuma shafi cikin gida, to mun jima muna sonyin maganar amma duba da yanda zaka d'auki maganar yasa mukayi shiru, yanzun ma mu fara jin jita-jita ne a gari da kuma labari daya zo mana daga wasu masarautun na magaganu da ake ta yad'awa akan ka, shiyasa muka ga hakk'inmu ne mu sanar da kai abinda ke faruwa." Wata lallausar ajiyar zuciya yayi ya kallesu a tsanake cikin fitar da kowace kalma a bakinshi yace "Liman, waziri, kar kuji komai ku fad'i abinda ke ranku, ina kallonku ne kamar iyaye na, kuna da damar sakani nayi abu ko bana so." Cike da jin dad'i waziri yayi murmushin gefen labb'a ya k'ara gyara zama yace "Mai martaba dama magana ce akan aure, kamar yanda kasan dokar garin basraba ta bawa mace damar yin mulki in har tana da aure, to haka ma dokar basraba ta bawa sarki damar auren mace biyu, uku, hud'u, amma mata d'aya bata dace da sarkin wannan gari mai tarin albarka ba, yanzu haka tsegumin da al'uma keyi kenan da ma wasu masarautun ana cewa sarki ya karya doka ta hanyar zama da mace d'aya har na tsewon shekara goma sha biyar, shine muka ga ba zamuyi shiru ba al'umar gari su ci gaba da tsegumi akan masarautar nan ba tare da munyi yunk'urin dak'ile matsalar ba." Shiru yayi kansa k'asa yana tunani akan abinda suka fad'a, tabbas gaskiya ne shi kanshi yana tunanin k'ara aure ko da zuciyarshi na son *Ameera* ne kad'ai, amma kuma ganin matsalar mata da ba'a rabasu da kishi musamman yanda suke k'azanta shi idan ance sun had'u gidan sarauta ko wani babban gida, shi shaida ne akan irin kishin da matan mahaifinshi keyi da mahaifiyarsu, duk da sun gamsu shine magajin sarki amma kuma suna bak'in ciki da hakan, kawunansu shi da yan uwanshi ba a had'e yake ba saboda yan ubanci, to wannan ne yake mishi shamaki da tunanin k'ara aure sai yaji yafi so yayi ta zama da Ameerarsa kuma sarauniyarsa, yana cikin tunanin abun fad'a musu liman yace "Ranka shi dad'e ba abu bane na ujila da muke buk'atar jin amsa daga bakinka yanzu yanzu, zamu koma mu, lokacin daka yanke shawara ma ji." Waziri da sam maganar liman bata masa dad'i bane ya kalleshi, tsaki yayi a cikin zuciyarshi saboda takaici, shi fa burinshi yanzu bai wuce ace 'yarsa ta shigo gidan sarauta ba a matsayin matar sarki, kuma yayi sa'a *uwar d'aki* (mahaifiyar Imran) har yanzu bata son Ameera saboda ganin basu dace ba, shiyasa ma ta k'arfafa masa gwiwa kan su tuntub'e shi da maganar k'ara aure, ita ko ta mishi magana zai shawarci *takawa* (har yanzu suna kiran tsohon sarki da wannan sunan), kuma takawa zai bashi zab'i ne yayi idan yana so idan baya so ya bari, uwa uba kuma 'yar uwarshi Sameera kuma mai bashi shawara akan harkokin mulki dama na cikin gida, ita kanta zata zame musu matsala, dan hakane ya taho da liman dan su mishi magana saboda yana matuk'ar ganin girman liman saboda mutum ne da babu wanda yake shakka in banda ubangijinshi, zuwansu tare ne zaisa ya yarda da duk abinda suka fad'a ya kuma gamsu, muryar sarki ce ta dawo dashi daga duniyar tunani yana fad'in "Liman na yarda da bayaninku, amma duk da haka zanyi shawara, duk abinda na yanke zaku ji." Da girmamawa liman ya amsa da "Allah ya shige mana gaba, Allah ya k'ara maka lafiya da nisan kwana." Mik'ewa yayi yana fad'in "Mun barka lafiya ranka shi dad'e." Mik'ewa waziri yayi yana bin bayan liman da harara, shi da ya so ayi komai a k'are yau d'in nan, amma gashi ya mishi shamaki da matsayin dake tunkaro shi, suna fita ya mik'e ya d'auki babbar alkyabarshi ya saka ba tare daya d'ora hular ta ba, cikin tako d'aid'ai ya tunkari k'ofar fita, yana isa k'ofar fadawa biyu ne tsaye suka sunkuya suna masa kirari, wucewa yayi suka take masa baya, duk da dare ya fara yi amma har yanzu ana kai da kawowa gidan, iya hangenka iya girman gidan, a haka ya isa b'angaren tsohon sarki wanda yanzu baya komai sai zaman gida da bawa mutanen gidan karatu, dan har yanzu jikinshi babu kyau tun rashin lafiyar daya kwanta sakamakon rashin sanin inda d'an uwanshi da yarshi suke, kamar yanda baya buk'atar k'yale k'yalen duniya hakan yasa ko mai gadin shiga k'ofar shi babu, Imran kuma dama kai tsaye yake shiga wajen mahaifin nashi, dan haka yanzu ma suna kawowa ya dakatar da fadawa shi kuma ya k'wank'wasa k'ofa, yaye labulen yayi dan tunda yaga k'ofar bud'e yasan zai iya shiga kai tsaye, zaune ya hango Musayyib ya tank'washe k'afafun shi da wani babban littafi a gabanshi yana karatu, yana ganinshi ya rufe littafin yana sakin murmushi da fad'in "Imaran kai ne yanzu? Zo zauna nan." Har Imran ya zauna shima yana murmushin, saida ya gama daidaita zama kamar yanda mahaifinshi yake kafin ya kalleshi yace "Ni ne Abba, Abba na karatu ake?" Da murmushi ya amsa da "Kamar dai kullum." "Allah ya k'ara maka lafiya Abba na, Allah ya k'ara maka nisan kwana." Murmushi yayi sosai yace "Imaran, ko yanzu na mutu Alhamdulillah, na rabu da iyayena lafiya, nayi mulkin jama'a kuma na tabbatar ban bar hawaye a idon talakana ba sai wanda ubangiji bai bani ikon saninshi ba, ina zaune da ku lafiya, to ni kuwa me zan nema a wata doguwar rayuwar?" Ba tare da murmushi ya bar fuskar Imran ba yace "Hakane Abba, ina fatan Allah yasa na kamalta mulki irin naka." Shi ma da murmushin yace "Kana kamaltawa Imran, labari na zuwa min na duk abinda ke faruwa, sai dai fatan a gama lafiya a kuma tabbata a haka." D'an kallonshi sarki yayi yace "Abba na magane ce dani a baki na, bansan ko kuna da lokacin da zan iya fad'a muku ba?" "Imran ka d'auka lokacin nan nawa na kane, kai ba ma wannan ba kad'ai gaba d'aya lokacin daya rage min na sauran rayuwa ta." Murmushi ya sake fad'ad'awa dan ko ba komai yana jin dad'in zamanshi tare da mahaifinshi, duk wata kalma da zata fito daga bakinshi mai dad'i ce, uwa uba ya kirashi da sunan Imaran, dan inba gabanshi ya zo ba baya jin wannan sunan, daga ranka shi dad'e sai mai martaba sai Allah ja zamaninka da sauransu, hakan yasa yake jin dad'i idan ya tuna a duniya akwai wanda ke kiranshi da Imran sak, dan ko mahaifiyarshi bata kiran sunanshi musamman daga lokacin da aka d'ora shi mulki zuwa yanzu, wani lokacin yana ji kamar tana sakaya sunanshi ne saboda ta tusawa abokan zamanta takaici, wani lokaci kuma kamar harda alfahari. Gyara zama yayi ya fara masa bayanin abinda su waziri suka fad'a mishi tare da cewa yana neman shawararshi. Bud'ar bakin tsohon sarki cewa yayi "... *Mu tara a shafi na gaba insha Allah, shin zai ce yayi aure ne ko kuma a'a? Wa ma za'a aura masa ne? Ya kuma zaman zai kasance?.* ✋ 29/05/2020 à 11:19 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _6_ Kallonshi yayi yace "To, ban gane me kake nufi ba?" "Yanzu zan fahimtar da kai Baba." Ya fad'a yana gyara zama sosai, ba tare da tsoron komai ba ko fargaba yace "Ni mutum ne daya yarda da tsafi, ina da wanda yake jib'antar al'amuran rayuwata (boka fa yake nufi), akwai wata babbar harka dana saka a gaba nake son ganin na cimma burina a kai, amma ya fad'a min komai zai tafi daidai da zaran na samu budurwa ina nemanta ta duburarta, ya kwatanta min kalar yarinyar dama fallasa min kamaninta, ina ganin yarinyar nan kuma na tabbatar ita ce, na fad'awa boka na kuma ya tabbatar min ita ce silar k'ara bunk'asar arzik'i na, amma komai zai tafi yanda ake so ne idan na fad'awa iyayenta komai da ita kanta yarinyar, dan ana buk'atar ku sani sannan ku amince d'ari bisa d'ari, wannan shine ya kawoni gareku, idan baku amince ba to ku sani kunyi asarar babbar dama, dan akan harkar nan a shirye nake dana kashe kud'i daga million d'aya har million hamsin, indai buk'ata zata biya." Kawu Mamu da yana saurarenshi gumi ne ke keto mishi, a zuciyarshi addu'a yake su rabu lafiya dan ya fahimci k'aton matsafi ne, amma yana jin million ta fara magana saiya kalleshi da sauri ya goge zufar yace "Million hamsin fa kace d'an nan? Kuma zaka iya bada su?" Wani shak'iyin murmushi yayi yace "Sosai ma, zan iya yin komai domin ganin na samu abinda nake so." *Allah ka mana tsari da irin mutanen nan, kawu Mamu ma ba iyaye ne da zakayi alfahari dasu ba, ko ba 'yar daka haifa ba ace mutum ya fito gwaro gwaro ya fad'a maka k'udirinshi akan wani naka, ina ga sai inda k'arfin ka ya k'are, abun kamar a almara amma kuma ya faru, ana irin wannan tab'argaza me zai hana ubangiji yayi fushi damu har ya dinga jarabtarmu da masifu iri-iri, Allah mun tuba ba dan hallayenmu ba ka mana gafara, domin kuwa kai mai gafara da kuma jin-k'ai.*👏 Cikin jin dad'i kawu Mamu yace "Wannan ai ba komai bane, dama ba ni na haifeta ba 'yar d'an uwa na ce, dan haka indai har zaka bayar da wannan kud'in to a shirye nake dana saka ta tayi maka duk abinda kake so, kuma dama ai yarinyar tana 'yan yawace yawacenta, kaga kuwa abun ba zai bata wahala ba." Duk da hausar tashi da k'yar yake ganeta amma dai ya fuskanci abinda yake nufi, dan haka ya kalleshi yace "Ka amince kenan?" Cikin sautinshi na fulatanci yace "K'warai kuwa Alhaji." Jinjina kai yayi alamar gamsuwa tare da saka hannu cikin aljihu, wasu sababbin kud'i ya fito da su yan jaka goma goma ya dire mishi gabanshi yana fad'in "Ga wannan naka ne, ka fara rik'ewa kafin na sake dawowa." Sake zura hannu yayi wani aljihun ya zaro wanda suka ninka waccen ya aje mishi yace "Wannan kuma a bawa yarinyar tayi buk'atunka, ta kuma tabbatar duk abinda zatayi zatayi shine dan gyaran jikinta saboda anfani na, ni zan tafi yanzu, zan dawo nan da sati d'aya lokacin nasan ta gama gyaran kanta." Yana fad'a ya mik'e ya saka takalminshi, kawu Mamu da tuni hankalinshi ya tashi kud'in ya d'auka yana waiwayen bayanshi yana zubawa aljihu, ganin bai ma san me yake ciki ba yasa ya wuce kawai ya barshi, saida ya bud'e murfin motar ya juyo yace "Sunan yarinyar Zeituna ko(dan bokanshi ya fad'a mishi a daren jiya)?" Cikin kid'imewa kawu Mamu yace "Eh Eh, sunanta kenan, Zeitu ba." Shiga kawai yayi ya tayar ya wuce, kawu kuma cikin gidan ya shiga Jumma na ganinshi tace "Yanzu Baban *Jumare* a waje ka baro mana tabarmar salan wani ya d'auke?" Da yatsa ya mata alama tayi shiru sannan ta biyoshi, bukkarshi suka shiga har saida ya sake labule kafin ya kalleta kamar marar gaskiya yace "Ke ba tabarma ba ki fad'i abinda kike so ma zan miki, zauna ki saurare ni kiji." Zaunen tayi tana kallonshi da tambayoyi pal a ranta, nan fa ya kwashe komai ya fad'a, al'ajabi tare da jinjina rashin imanin mijinta ne suka rufeta, da mamaki ta kalleshi tace "Baban Jumare, yanzu kuma kai ka amince da nufin mutumin nan a kan 'yar d'an uwanka? Baka tsoron abinda mutane zasu fad'a? Sannan ba ka tunanin ma ko kasheta zasuyi? Haba ka duba lamarin nan mana." Rufe ido yayi ya fara zazzaga mata bala'i wai 'yar d'an uwanshi ce ai, sannan kullum ita ke fad'a mishi Zeituna karuwanci take, to meye yanzu dan anzo har gida an nemi izininshi, ita dai hankalinta bai kwanta ba har saida yace "To wallahi idan ba zaki bani goyon baya ba sakinki zanyi, kinga dai yanzu ina da kud'i? Dan haka k'ara aure ba zai min wahala ba." Sai lokacin kad'ai ta wayance ta nuna mishi ba komai kawai, kud'i ya tsakuro ya bata yace "Wannan kuje kusuwa ke da ita idan ta dawo ki siyo mata kaya masu kyau na kwalliya da ado, wannan kuma kema kya fara tab'awa." Ya fad'a yana d'auko jaka goma ya bata, ai sai taji kamar ya bata duniya, nan fa suka shiga bushasha da kud'i anata farin ciki. *Misalin 08:07 na dare* Tunda Hajia na gidan shiyasa yau Zeituna bata tsaya cikin gidan ba, tare da Iya suka fito kowa yayi hanyarshi, amma tana ganin Iya ta b'ace ma ganinta saita lab'e a cikin kwanar ta zauna anan, lieutenant kawai take so ta gani sannan ta wuce gida, duk motar da taji tayi oda a k'ofar gidan saita lek'o da sauri, amma sai taga wani ne daban ba shi ba, a k'alla ta d'auki minti kusan ashirin bai dawowa sai kawai ta yanke shawarar tafiya, dan bata so tayi dare irin na jiya na jawa kanta masifa, mik'ewa tayi jiki a sanyaye ta kama hanya duk zuciyarta babu dad'i, da haka ta isa gida tana zuwa kuma mamaki kuma ya nemi halakata saboda Inna Jumma ce da kanta ta bata tuwo, inda kawu kuma har yake tambayarta ta k'oshi? Jumma ce tace "Tashi ki d'ibi ruwa kiyi wanka ki zo zaki rakani unguwa." Da mamaki ta kalleta tace "Unguwa kuma Inna?" "Eh." Tashi tayi tana mamakin canzawar mutanen, ta zauna tare da su na tsawon shekara goma sha biyu, amma abu makamancin wannan bai tab'a faruwa ba sai yau, to me suke nufi? Ta tambayi kanta, kar azo ko salwantar dake zasuyi ma dan su huta, wata zuciyar ta fad'a mata haka, da wannan wasi-wasi ta samu tayi wanka sai dai babu wani sabulu mai kyau, haka ta fito suka shirya suka fito, adaidaita suka samu ta kaisu kasuwa ta aje, kayan kanti ta siya mata saidai ba masu yawa ba, saboda tsadarsu yasa basu iya d'aukar dayawa ba, daga doguwar riga uku sai riga da siket biyu, kayan kwalliya ta siya mata aka had'a da sabulu da man goge baki da sabi takalma masu tsini, daga nan suka wuce gida Jumma na ji a ranta ita ma fa ta waye, alhalin duk kayan da ake siye babu wanda ake yayinshi yanzu duk tsofaffin yayi ne, amma a haka take ganin ita ma ta zama cikakkiyar yar birni. Zeituna kasa bacci tayi da suka ce wannan kayanta ne, ta nemi tasan dalilinsu na canzawa amma kawu Mamu yace ai d'iyarshi ce ita ma, zai iya yi mata komai kamar yanda zai wa su Jumare, wanda a wannan lokacin Jumare dake kamar k'anwa ga Zeituna dan ta bata shekara uku haushi kamar zai kasheta, har d'aki ta samu Jumma tana kuka wai an yiwa Zeituna siyayya ita ba'a mata ba, nan ta bata hak'uri tace ita ma gobe zata amshi kud'i wurin babanta a siyo mata, da haka kad'ai tayi shiru ta koma d'akin su, haka tayita hattarar Zeituna tana zaginta tana harara tana mata cilli da kayan da aka siyo, saida kawu Mamu ya mata magana daga cikin bukkarshi yace zai ci uwata kad'ai ta shafa mata lafiya. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Ko da Junaid ya zo gida shiryawa yayi ya sake fita, bai zame ko ina ba sai gidansu Maryama, yana zuwa kuma sun fita ba jimawa, amma yayi nasarar ganin Huda a k'ofar gida da madara tana sha, hannunta ya kama yace "Huda ko?" Kai kawai ta d'aga mishi, murmushi yayi yace "Ina mamanki?" Saida ta kalli hanyar dasu Maryama sukayi tace "Yanzu suka fita ita da tanti Iklima." Nuna hanyar yayi yace "Kenan ta nan suka bi?" "Eh." Ta fad'a tana sake d'aga mishi kai, mik'ewa yayi yasa hannu aljihu ya ciro jaka goma guda ya damk'a mata a hannu yace "Wannan kisha madara kinji ko." Da sauri ta fizge hannunta ta sakar masa kud'in tace "A'a bana so, Mamata ta hanani karb'ar kud'in maza." Da mamaki yace "To me yasa?" Tana kallon idonshi tace "Tace wai ita zatayi aiki dan ta samo min komai da nake so." Murmushi ya sakeyi ya k'ara mik'o mata kud'in yace "To ki karb'i wannan, ni bana cikin wanda ta hanaki karb'an kud'in su saboda ni mahaifinki ne." Zaro ido tayi tace "Kaiii, ni fa bana da Baba, mutane ma ce min suke shegiya, kuma suna cewa mamata yar iska ce." Jim yayi saboda rashin jin dad'in abinda ya fito daga bakin yarinyar, murmushin yak'e ya mata yace "To yanzu dai karb'i wannan, insha Allahu lokaci yayi da zaki ga mahaifinki kema." Mak'ale kafad'a tayi tace "Um um, idan na amsa Mama zata toye min hannu na da wuta." Lura da yayi ba zata karb'a ba yasa yace "To shikenan, yanzu fad'a min me kike so na siyo miki idan zan dawo." Rufe baki tayi tsoro ya bayyana a tare da ita tace "Dan Allah karka fad'awa Mama na nayi hira da kai, ta hanani tsayawa da maza a waje." Tana gama fad'a ta ruga a guje tayi cikin gidan, da kallo ya bita shi kuma yana mamakin yanda Maryama ke tsaye kan tarbiyyar 'yarta, amma kuma ita tana zubarwa da yarinyar mutumci, motarshi ta shiga ya nufi inda yasan zai ganta, bai kuwa sha wahala ba ya samu Iklima zaune bakin wani dakali a pacific tare da wani, fitowa yayi suka gaisa ya tambayeta ina Maryama? D'akin dake bayansu ta nuna mishi tace "Tana ciki, amma tana fitowa yanzu." Kallon d'akin yayi yaji zuciyarshi na neman bugawa, ji yayi kamar ya tura k'ofar ya shiga, amma kuma tsoron abinda zai gani yasa ya kasa hakan, tsayuwarshi kuma ya jirata shi ma dai wani k'arin tension d'in ne, juyawa yayi ya bud'a mota zai shiga sai yaji an fito daga d'akin, juyowa yayi sai kuwa suka had'a ido, sam bata cikin yanayin farin ciki dan fuskarta a had'e take, bayanta wani matashin yaro ne ya fito da ba zai wuce shekara ashirin da d'aya zuwa da biyu ba, Maryama kuma a k'alla ba a k'asara ba tana da shekara ashirin da shida zuwa da bakwai, zai iya kiranta warin k'anwar shi Umaima, wani buhun haushi ne ya rufe shi ya tsaya yana kallonta harta k'araso kusa da Iklima, wannan matashin kam sai wasar baki yake ya bawa d'aya abokin na shi hannu yace "Saura kai, amma ba zan jira ka ba gaskiya." Mik'ewa shi ma yayi ya shiga d'akin sai Iklima data juyo ta kalli Junaid tace "Yallab'ai Junaid sai anjima." D'akin ta shiga yana kallo suka rufe, zaune Maryama tayi bakin dakalin ita ma dan jiran Iklima, shi kuma waccen matashin ya wuce Junaid ya bishi da kallo kamar ya shak'e shi, amma ya zaiyi duk abinda ya samu shamuwa watan bakwai ne ya ja mata, kallonta yake kamar zai had'e ta ita kuma ta had'e fuska tana danna wayarta, rufe murfin motar yayi ya tako ya zo gabanta, cikin wani yanayi yace "Yanzu dan Allah Maryama baki ji kunya ba?" A hankali ta d'ago kai ta kalleshi tace "Kunya kuma? Ta me fa?" Girgiza kai yayi yace "Maryama me waccen yaron zai miki? Idan dan kud'i kike siyar da mutumcinki na baki kud'i Maryama dan ki tsira daga rainin irin wannan yaran, idan kuma dan jin dad'i kike bud'a farjinki ga kowane d'a namiji, domin Allah me waccen zai iya yi miki? Me zai hana ki nemi cikakken namiji wanda zaki san ya shige ki har ma ya sakaki kukan dad'i ko na wahala, amma waccen da ko kaciyarshi bata gama warkewa ba tsiyar me zai tsinana miki? Ni fa da aure nake sonki, Maryama dan Allah ki taimaka ki aure ni ko na kwana d'aya ne, ni kuma zanyi k'ok'ari na ga na gamsar dake ta kowane fanni har ki yarda ki zauna dani, amma wannan abun kunya dame yayi kama, yaron da na tabbatar kud'in daya biyaki shi kanshi k'uru ce yayi ya baki su saboda shed'an na k'awata mishi yin zinar, mtssss." Duk da ba cikin hargagi yake maganar ba amma ta tabbatar ranshi ne ya b'ace, mik'ewa tayi ita ma cikin b'acin rai da fitar da hawaye a idonta tasa hannunta ta fito da kud'i a rigar nononta ta warware su, jaka biyu ce nuna mishi tayi tana fad'in "Kaga abinda ya bani, wannan kuma zan ci abinci da su na tsawon kwana uku ni da 'yata, malam ka fita a harka ta mana, soyayya ce nace banayi ka shafa min lafiya mana, ko ana so dole ne?" Sai kuma ta fashe da kuka ta koma ta zauna kamar an turata, cikin kuka ba tare data kalleshi ba take fad'in "Taya kake tunanin zan ji dad'in rayuwata? Taya kake tunanin ina farin ciki da abinda ke faruwa da ni? Waccen yaron fa bai fi sa'an k'ane na ba na biyu, amma yau ni ce na kwanta yaron can ya nemi yanda yake so, meye anfanin rayuwa ta Junaid? Me yasa iyayena zasuyi min haka? Me yasa wannan mutumin da ko sunanshi ban sani ba ya tafi ya bar ni da 'yarsa? Me ya kamata nayi yanzu? Junaid ka fahimci wani abu, duniya yanzu ba'a taimako dan Allah sai dan abinda zaka bayar ko za'a samu daga gareka, da irin hakane aka lalata min rayuwata, kuma da hakanne ma yanzu ake ci gaba da gurb'ata min rayuwar." A hankali ya zauna akan dakalin cikin sanyin jiki ya kalleta yace "Maryama rayuwarki na da anfani, kuma tabbas yanzun rayuwarki a gurb'ace take, amma idan har kin so canzawa kuma kika bani dama wallahi zaki dawo sabuwar mace kamar babu abinda ya tab'a faruwa dake, dan Allah Maryama ki amince da soyayya da nake miki, wallahi babu nufin cutarwa ko sharri a zuciyata, ni zan zama miji na gari a gareki, sannan zan zama uba da za ayi alfahari da shi ga 'yarki Huda, ki amince ki bani linzamin ragamar rayuwarki, zan d'aukeki na kaiki cikin ahalina kuma farin cikina, kema zaki zama d'aya daga cikin dangina." Shiru tayi sai yar shashek'ar kuka da take tana tunanin abinyi, tabbas tun zuwanta garin nan a cikin manya manyan mutanen da take jin labarinsu a gari akwai ahalin Gaga, wanda suke ji da iko, matsayi, da kuma naira, ahali ne daya tara yan boko sosai kuma bokon ta musu rana, matsalarta d'aya shine tana jin tsoron shiga cikin babban dangin irin wannan saboda abinda ka iya zuwa ya dawo, tana cikin wannan tunanin Iklima suka fito suma, saurayin wucewa yayi inda Iklima ta kallesu tace "Mari kina nan dama? Ai na d'auka kin tafi da naga mutumin na ki ya zo." Mik'ewa tayi tana k'ara share hawaye tace "Mu tafi kawai." Wucewa tayi ita kuma zata wuce Junaid yace "Iklima dan Allah zan iya sanin labarin Maryama? Dan na fahimci abun na damunta kuma kamar tana yi ne ba da son ranta ba." Rik'e hab'a tayi tace "🤔 Ni! Rufa min asiri, wallahi ba zan iya fad'a maka komai ba a game da ita har saita bani izini." Kallonta yayi yace "Bima'ana dai kinsai komai?" "K'warai kuwa na sani." Saida ya kalli Maryama dake tafiya ko d'an kwali babu a kai sai riga da siket d'in ta na atamfa ko waiwaye babu yace "To dan Allah inhar ke masoyiyarta ce ta gaskiya ki fad'a min asalin Maryam, ma'ana garinsu, iyayenta, inda da inda suke zaune, idan kika min haka kin gama biyana a rayuwa, ni kuma zan tabbatar na gyara rayuwar k'awar ki da yardar Allah." Ajiyar zuciya ta sauke tace "Ina k'aunar Mari, kuma ina sonta da shiriya kamar yanda nake so wa kaina, ni labari na bai kai na ta muni ba, dan ni na fito ne da son raina, hasalima ina gari d'aya da iyayena, amma ita na ta labarin akwai tausayi ciki, kuma sau da dama ina cewa ta sake komawa gida, watak'ila mahaifiyarta ta yafe mata, amma sam bata saurare na saboda tayi hushi ita, dan haka zan fad'a maka komai daya shafeta ko da hakan na nufin zamu samu matsala, nasan daga baya zata fahimce ni kuma ta yafe min." *Bara muji tarihin Mari.* Nuna mishi dakalin tayi tace su zauna, bayan sun zauna ta saita nutsuwarta tace "Maryama 'yar asalin garin *Gouré* ce dake yankin *Diffa*, tana rayuwa kamar kowa ita ma tare da iyayenta, ita kad'ai suka haifa a duniya, dan haka suke matuk'ar sonta musamman mahaifinta, tana samun duk wani abu da take so a duniyar nan, mahaifinta na nuna mata gata duk da cewa ba mai k'arfi bane, tana karatunta na islamiyya da boko, suna tsaka da rayuwarsu cikin farin ciki wata rana mahaifinta yayi had'ari da moto, munanan raunikan daya samu ne suka jaza mishi kwanciya jinya na tsawon shekara biyu kwance a gida, k'afafun shi basa takuwa haka ma ko zama baya iya wa sai kwanci, wannan rashin lafiyar tashi ita ta jijjiga Mari da mahaifiyarta, ta kai ta kawo sun cinye duk wani abu da suke da shi, yan uwa kuma babu mai k'arfin da zai iya d'auke musu wannan nauyin, sun shiga matsi da takura ta yanda Mari har karatunta ya samu matsala, da haka suke rayuwar babu dad'i, rana tsaka sai wani ciwon ya taso mahaifinta a gaba, bayan sun kaishi babbar asibiti ne aka tabbatar musu da hantarshi kuma ta samu matsala, yana buk'atar aiki da gaggawa, haka ma k'ashin bayanshi a karye yake, da k'yar dangi aka samu aka biya kud'in da aka mishi radion (scanning) d'in ma, hakan yasa ido suka raina fata akan kud'in da za'a mishi aiki, gashi ance aikin hantar sai a *zinder* za ayi, kwanansu biyu a asibiti suka ce zasu sallamesu tunda basu da niyyar biyan komai, a yammacin ranar Mari tayi kuka sosai saboda ikrarin da sukayi na sallamarsu, bayan sallah magriba mahaifinta ya dinga wani abu kamar na fitar rai, hakan yasa hankalinsu tashi Mari tana kuka tace ita zata fita ta nemo kud'in, babu wanda ya kula da ita saboda kowa ya rud'e, tana fita kuma ana iska hadari ya had'e gari, sam wannan bai dameta ba haka ta d'auki hanya ba tare da sanin ina ta dosa ba, tayi tafiya mai tsayi aka sako da ruwa kamar da bakin k'warya, ruwa ake sosai tare da iska mai k'arfin gaske, kan hanya babu kowa sai motoci dake wucewa suma ba akai akai ba, duk motar da ta zo wucewa haka zata daga hannu tana neman su tsaya, amma babu mai kallonta bare tasa ran a taimaketa, cikin hakane wata k'aramar mota mai kyau ta zo wucewa a hankali, kamar a mafarki tana d'aga mishi hannu harya wuce sai kuma ya yo baya baya ya tsaya, saurayin matashi ne a cikin motar da ganinshi kamar mai hankali, zuge glas d'in motar yayi ita kuma ta lek'a cikin kuka tace... "Dan Allah malam ka taimake ni kamar yanda Allah ya taimake ka, mahaifina ne bashi da lafiya yana asibiti kwance, ka taimaka min dan Allah karya mutu." Kallonta yayi yace "Wane asibiti yake." Da sauri tace "Babba, babba ce." Jim yayi kafin ya bud'e mata k'ofar yace "Shigo muje ko." Da sauri ta shiga ta ja k'ofar ta rufe, kallonshi tayi tana tattare hijabinta tace "Nagode." D'an motsa bakinshi kawai yayi ya tada motar ya wuce, ita kuma sai tattare kayanta take saboda a jik'e suke sharaf har zuba ruwan keyi, yanda suke tafiya a hankali haka ma rywa suke fara dama dama, amma abinka ga ruwan sama sai kuwa wasu ruwan suka sake gabcewa da k'arfinda yafi na baya, hakanne ya tilasta mishi paka motar ya kalleta yace "Ruwan nan sunyi k'arfi dayawa, mu jira su rage sai mu tafi." Kai kawai ta d'an jinjina mishi dan ita da a k'asa take babu abinda zai tsayar da ita, a hankali taga yana k'ara kwantar da kujerarshi baya idonshi a lumshe, da ganinshi zaka san kamar akwai abinda ke damunshi shima, lokaci lokaci sai Mari ta juya ta kalleshi amma shi idonshi rufe kamar zaiyi bacci, tunanin mutumin dake son taimaka mata shima a damuwa yake yasa Mari cewa "Mmm...ala..m l...afiy...a? Ko baka da lafiya ne?" Sam Mari bata tab'a fahimtar muryar da tayi magana da ita ba zata sake d'aukar hankalin mutumin, a hankali ya bud'e ido saboda yanda tayi maganar ya sake tayar mishi da tsikar jikinshi, tasowa yayi daga kwanciyar da yayi ya sake kallonta zaiyi magana, sai kuma ya kalli jikinta wanda ke jik'e da ruwa duk jikinta ya bayyana, duk da zaune take amma saida ya sake jin wani abu, take a wurin shed'an ya fizge shi yaji ya rasa duk wani k'arfin kare kanshi daga abinda zuciyarshi ke raya mishi daya aikata. A hankali ya kai lallausan hannunshi ya jawo hannunta da yayi sanyi saboda ruwa, bai sauke hannunta a ko ina ba sai kan hantsar wandonshi, yana jin tafin hannun mace ya sauka a inda ke mishi k'aik'ayi sai kawai ya lumshe ido ya sake matse hannunta had'e da nashi hannun, ita kuma da tsoro ya rufeta fizgo hannunta tayi tare da sakin k'ara, da sauri ya kalleta idonshi jawur dasu sai lumshesu yake, cikin k'ak'aro magana yace "Bbbbanda lafiya, ki ta...ima..ka min." Cikin firgici ta juya da k'arfi ta kama hannun motar zata bud'e ashe tun shigarta ya rufeta ruf, juyowa tayi ta fashe da kuka tace "Dan Allah malam kayi hak'uri karka cutar dani, neman taimakon ne na..." Yanda ya k'ura wa bakinta ido da fuskarta ne yasa yake ayyana kyawunta, bai bata damar k'arasawa ba ya fizgota ya had'e bakinshi da na ta, matseta yayi sosai a jikinshi yana kiciniyar yaye mata hijabi, dukanshi ta fara da hannayenta tana tura shi baya tana so ta raba bakinsu, yana jin haka amma kamar bashi take duka ba duk da kuwa har abincinshi take kuma yana jin zafi, sam baya hayyacinshi bare ya fahimci warin da kanta keyi wanda baya samun gyara saboda rashin kud'i gashi kuma ruwa sun dake shi, yanda suke kokawa yasa bai iya cire mata hijabin ba, dan haka ya kwantar da kujerarta ya bi kanta ya taushe ta, yanda take bille bille da neman taimako ne yasa ya raba bakinsu ya kaishi saitin kunnanta ya rad'a mata "Kiyi shiru ke, ba wani abu bane ba, ni zan taimaki mahaifinki har ya samu lafiya, zan baki kud'i masu yawa idan kika barni, kuma fa ke kika tambayeni..." Yana cikin maganar kuma yake fito da kayan aikinshi😎da hannu d'aya, hannun yasa ya janye siket d'in ta yasa hannu ya shafi cinyarta, jin hakane yasa ta mishi wata bangaza har saida ya kaiwa k'ofa karo, tashi tayi zaune tana neman hanyar arcewa, cikin jin zafi ya sake haye ruwan cikinta ya fara tattare mata siket d'in, ihu ta fara wanda yasa shi rufe mata baki da hannu d'aya, yanda ya sakar mata nauyi ta ji ko numfashi ba tayi da kyau yasa ta saduda cikin kuka tace "Dan Allah malam ka taimake ni kar ka cutar dani, ni fa taimako kawai na nema wurinka, mahaifina yana can rai a hannu Allah karya mutu bana kusanshi." A wannan lokacin hanya kawai yake nema, d'an wandonta daya sha jiki ya fizgoshi da k'arfi ya k'arasa cirewa, wani kukan tasa da k'arfi ta yunk'ura, k'ara dafe mata baki yayi yace "Shiiiii, ki kwantar da hankalinki kinji." Da k'arfi tace "Ba zan iya ba, wallahi ni ba yar iska bace, ban tab'a iskanci ba, ka dubi Allah ka rabu da ni." Cikin wata shegiyar murya yana cikin neman hanya yace "Babu komai fa a ciki, wallahi nima ba d'an iska bane, tsautsayi ne yasa ni kallon abinda ya d'aga min hankali, ke kuma sai kika shigo hanyata, hakan na nufin Allah ne ya sama min mafita, dan Allah ki nutsu kar kisa na ji miki ciwo dan wallahi ban tab'a yi ba." Cikin azababben kuka tace "Tsoro nake ji, ban tab'a yi ba, kai ni wallahi ban tab'a ganin yanda akeyi ba, kuma fa ance ta haka ake samun ciki na mutum." Jin abu na shafar ta a gabanta yasa ta sake rud'ewa tace "Idan fa ciki ya shiga jikina sakamakon hakan? Ya kake so na yi? Wai kai baka da imani ne?" Take Jibril ya danna kanshi cikin matancin Maryama ba tare da sadaki ba ko tunanin wani abu, cikin kuka ta furta "Wayyo zai kashe ni." Shi kam yana jin shi a sabuwar duniya sai kawai ya fara tafiyar da ita kamar wata mai ido bud'e, tsabar jarabar tashi a kusa take ko minti biyu baiyi ba ya samu sauk'i da nutsuwa, kwantar da kanshi yayi kan k'irjin ta zufa na keto mishi, Maryama kam tayi shiru sai kuka take na bala'in rad'ad'in da take ji a jikinta, jin baya da niyyar d'aga ta yasa ta tattaro k'arfin ta ta tureshi, yana d'agata sai yaji wata irin kunya da dana sani sun rufeshi lokaci d'aya, fita yayi daga motar yana gyara wandonshi duk da ruwan dake sauka jikinshi, kifa kanshi yayi jikin motar wasu hawaye ya fara yi na takaicin abinda ya faru, shi yanzu taya ma zai fara kallon yarinyarda ko sunanta bai sani ba, shin me zai fad'a mata ta yarda da shi? Ya zaiyi da ita? Da wane ido zai kalleta? Yana cikin son sanin amsar wannan tambayoyin yaji an bud'e mota an fito, da sauri ya d'ago idonshi yana k'yakk'yabta ido saboda ruwan dake sauka akai, yarinyar ya gani sai faman gyaran jikinta take tana k'ok'arin daidaita tafiyarta, da gudu yasha gabanta yana kallon fuskarta yace "... *Allah ka gafarta mana.*👏 29/05/2020 à 11:23 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _5_ "Yaranku fa ya fito da gwanarshi." A tare suka kalleta sai lieutenant da yayi saurin cewa "Ah da kyau, wacece wannan? Ina fatan dai yar gidan nan ce ko? Dan kunga muna da 'yan mata dayawa masha Allah, kamata yayi ace muna musu auren zumunci." Murmushi tayi cike da kunya tace "Ai kayanka ya tsinke a bakin kaba, domin kuwa ma a cikin 'ya'yanka ne." Cikin fara'a yace "Wai kina nufin 'yan biyu na?" Kai kawai ta d'aga mishi alamar eh, dukansu farin ciki ne ya bayyana a tare da su, suna tsaka da tattaunawa ita kuma harta juya zata tafi ta ji murya Zeituna tace "Aunty babu wani abu da za ayi? Gida nake son tafiya." Dukansu da mamaki suka kalleta banda colonel da ko kallonta baiyi ba, Soueba mamaki ne ya hanata magana, dan duk ma'aikatan gidan babu mai kwana anan sai *Nana* dake budurwa, ita ma kuma saboda ba 'yar garin nan bace, sannan wani lokacin Hajia na neman abun ci kuma tafi son na ta, amma banda ita duk sauran suna tafiya ne bayan sallah isha'i, amma ga Zeituna har goman dare kuma bata san tana nan ba sai yanzu, a cikin kallon da take mata ne na tuhuma ta fahimci hankali da idon Zeituna suna kan lieutenant, abun al'ajabin shine kallon da take masa yasa ta kasa fahimtar yanayin dake fuskarta, shin tsantsar *so* ne take hangowa ko kuma *k'auna* ce, wata k'akk'arfar ajiyar zuciya ta sauke ta saci kallon lieutenant d'in, amma shi sam baisan ma tanayi ba sai hirarsu suke, sake kallonta tayi tace "Ba komai Zeituna, zaki iya tafiya gida, amma ki kula dan Allah dan kinga dare yayi, kuma ke gashi unguwarku da duhu akan hanyar." Saida Zeituna ta k'ara kallon lieutenant sannan tace "To aunty, saida safe." Juyawa tayi zata wuce ta sake kafeshi da ido ta sunkuya tace "Abban Ammar saida safenku." Take ya kalleta shi da Labaran suka amsa da "Saida safe." Fita tayi daga gidan bayan ta sauke ajiyar zuciya, murmushi tayi sosai kamar mahaukaciya kuma saita dinga tsalle tsalle tana dariya harda juyi akan hanya tana farin ciki kawai saboda ta ga lieutenant kuma lafiyarshi k'alau, dan ita bata san tafiyarsu ba saida ta ankare daya wuce lokacin dawowarshi ne hankalinta ya fara tashi, shiyasa ta kasa tafiya gida tace ko zata kwana sai taga ya shigo dan ta tabbatar da lafiyarshi lau, tana cikin haka wani mai moto daya karyo kwana suka kusa had'ewa da ita, odar daya danna mata ce tasa ya dawo hankalinta, cak ta tsaya dan ta d'auke ma ya bige ta ne, masha Allah mai moton shi kuma da manyan idonshi kamar zasu fito waje ya k'ura mata ido, a ranshi yake ayyana kaga wani irin gamdakatar, yarinyar da nake nema gata na samu a cikin dare, duk da dai ya k'are mata kallo amma a wajenshi mai neman biyan buk'ata ba komai bane, tana samun kulawa zata wanke tayi fess, ita kuma sai lokacin ta dawo hankalinta ta tuna inda zataje, waro ido tayi ta dafe k'irji tace "Na shiga uku ni Zeituna, yau ya zanyi da kawu *Mamu*?" Haba ai saita wuce da sauri har da gudu gudu take hannu d'aya a kai tana fad'in "Nasan ma kashe ni zaiyi wallahi, oh ni Zeituna, soyayyar wanda baisan ina yi ba na neman haukata ni." Haba wannan mutumin da shima yake ganin ya samu abinda yake nema ai sai ya juya kan moton ya fara bin bayanta, dan in yace ya tsayar da ita ya tabbatar ba zata saurare shi ba dan alamu sun nuna sauri take, dan haka ya dinga binta har saida ta shiga wani layi dake da babban kwalbati gaban kwalbatin kuma katangu ne kawai wanda kake iya hango bukkokin ciki, d'aya daga cikin gidajen ta shiga wanda ke d'auke da bukka uku a ciki, yana ganin haka ya juya da moton shi da tunanin dawowa gobe da safe. Shiru gidan da alama sunyi bacci sai wani dattijo dake kan tabarmar kaba kusa da wata bukka da redio yana saurare, kamar wacce k'wai ya fashe ma a ciki haka ta k'arasa gabanshi ta durk'usa cikin harshen fulatanci tace "Kawu walijam? noi chomrii (ya gajiya)?" D'agowa yayi daga kwanciyar da yake ya sauke idonshi a kanta, kafin yayi magana ya d'auki k'aton takalmanshi na fata mai shegen nauyi ya mazga mata a fuska, Allah yasa bai sameta a kunci ba sai a goshi, taji zafi sosai dan haka ta dafe wuri ta fashe da kuka, cikin harshen fulatancin da yafi k'warewa akai ya fara zazzaga mata bala'i na daren da tayi, wannan surutun na shi yasa matarshi *Jumma* fitowa, maimakon bashi hak'uri sai ita ma ta dinga fad'in a harshensu "Ai dama na fad'a maka yarinyar nan karuwanci take zuwa, wani irin aiki ne zai tsayar da ita har wannan lokaci, ni fa tuni nayi nisa a bacci ace sai yanzu zata shigo gida, da k'ofa gare mu kenan saita bubbuga ta nunawa mak'wabtan mu ta dawo a zo a bud'e mata k'ofa, saida suka gama zageta ta uwa ta uba babu tunanin marainiya ce suke rik'o sannan 'yar d'an uwanshi sannan yace ta b'ace mishi da gani, ta tashi zata shiga bukkarsu wacce suke su uku a ciki ita da yaransu Jumma tace "Abincinki fa? Ko da yake ma ai nasan kin gama k'oshi a wajen yawon." Cikin kuka tace "Mihari (na k'oshi)." Kawu Mamu ne ya fara magana da hausa saidai a yanayin daya iya yace "Wane abinshi jaki bata? Ke ki shaurare ni ma da kyau kiji, wannan ishkanshin nata ya kusha karewa domin kuwa aure jan mata, janje kauyen *gwadojji* na shamo mata miji kafin ta ja min abun kunya, shannan na tsawon kwana uku ban lamunshe ki bata abincin gidan nan ba, ja ta shi ashan wajen yawon ishkanshin na ta." Dad'i Jumma taji hakan yasa ta juya zata koma bukkarta tace mishi " Jamwala (saida safe)." Tana shiga bukkar ba tare da damuwa ba ta cire hijabinta ta shinfid'a k'asa ko tabarma babu ta kwanta tana kallon yaran dake kan katifa duk da dai ba wata ta kirki bace, amma a wajenta da take kwana k'asa wannan d'in kamar gado ce na alfarma, tunanin iyayenta ta shiga yi wanda suka nuna mata gata da soyayya lokacin da suke raye, amma mutuwa ta d'auke su a lokaci d'aya sakamakon had'arin daya ritsa da su na mota, wani sabon kuka ta dasa ta ci ta k'oshi hata gode Allah kafin bacci yayi gaba da ita. *Gaga's falimy*😂 *10:30* na dare Amar dake zaune a falo suna kallo shi da duka 'yan uwan wayarshi tayi k'ara, yana dubawa ya d'auka yana fad'in "Ummy baki kwanta ba har yanzu?" Ammar dake zaune nesa da shi kamar zaiyi kwance yana latsa wayarshi ne ya kalleshi ta gefen ido, daga wajen Ummy ta amsa mishi da "Banyi bacci ba Amar, ka ci abinci ne?" Amsawa yayi da "Ban ci ba Ummy, bana jin yunwa ne." "A'a ban yarda ba, maza ka shigo ka samu wani abu ko marar nauyi ne ka ci, kai baka tausayin kanka ne da halin da kake ciki? To ka zo yanzu ina jiranka." Kashe wayar tayi shi kuma ya mik'e a gajiye yana fad'in "Ummy sai kace wani yaron goye, ni ba yunwa nake ji ba." Junaid ne yace "To ina laifin Ummy, kulawa fa akace yabawa, ta damu da kai ne shiyasa." Wani dogon tsaki Ammar yaja ya mik'e a hassale ya shige d'akin shi ya mayar da k'ofar ya rufe, da kallo suka bishi sai dai babu wanda ya damu bare yayi tunanin abinda yasa yayi hakan, fita Amar yayi a farfajiya ya had'u da Jibril ya dawo a matuk'ar gajiye, gaisawa sukayi kafin shi ya wuce babban falo shi kuma nasu falon. Ammar na shiga cilli yayi da wayarshi kan gado ya fad'a ban d'aki, ba jimawa ya fito ya watsa ruwa ya kashe wutar d'akin ya kwanta daga shi sai gajeran wando, kifa kanshi yayi tsakiyar pilow yana k'ok'arin ya cire damuwar nan a ranshi, baya so abun ya dinga damunshi amma ya zaiyi mutum ne shi mai zuciya da jini, jin baccin na neman gagararshi yasa ya mik'e ya b'allo maganin bacci, a k'a'ida damuwarshi bata kai yasha guda d'aya ba, rabi ya kamata yasha, amma saboda haushi yasa yasha guda d'aya sannan ya kwanta, ai kuwa baifi minti sha biyar ba kwana ya d'auke shi marar dad'i sai dai mai k'arfi. *Washe gari* Kamar ibada yau ma hakane a wurin Zeituna, tana yin sallah asuba ta shiga d'ebo ruwa a panpo, layin data tarar yasa har gari yayi haske kafin ta samu ta turo kurar ruwan mai d'aukar jarka (bidon) takwas, da kanta ta dinga saukewa tana shigar da su tana juyewa a randa da tuluna da manyan bokitai, saida ta gama cas sannan tayi wanke wanke, data wanke ne ta samu ta d'ora d'umamen tuwon masara wanda miyar kukar taji daddawa, kafin yayi zafi ta gama sharar tsakar gidan, tana idawa ta zubawa duk wanda tasan tana zuba ma ta kai musu, tana dawowa babbar buta ta d'auka ta fara d'iban ruwa dan tayi wanka, amma Jumma na gani ta fito tace "Me ja kiyi da wannan ruwan?" Cikin marairaicewa tace "Inna wanka nake so nayi , kinga fa yau kwana hud'u kenan baki barni nayi wanka ba, har Hajia ta fara min magana akan k'azantar jiki na." Fizge butar tayi ta juye mata ruwan a jikinta tace "Ba ja kiyi ba, na ce ba zakiyi wankan ba marar mutunci kawai, ki wuce ki tafi hakanan in kuna son zuwa kafin nasa kawunki ya dakatar dake." Cikin muryar kuka tace "Dan Allah Inna to ki bari na ci abinci saina tafi." Da k'arfi tace "Abinci? Har abincinki ma kika fitar? To kiji da kyau jiya kawunki yace kar na sake baki abinci har na kwana uku, dan haka ki wuce ma karki wahalar da kanki." Takawa ta fara yi cikin fitar da hawaye tana matse hijabinta wanda dattinshi yasa take sanyashi a birkice, yanzu gashi ruwan data zuba mata yasa duk wani tsohon datti da wari ya taso, ita kanta sai take jin k'yank'yamin kanta, tana zuwa ta ja kurar ruwan dake k'ofar gidan ta nufi wajen aikinta da ita, saboda tafiyar dake akwai dama yasa ta fad'awa mai kurar zata dinga kawo mishi in zata je wurin aiki, tana tafiya tana share k'walla harta isa ta aje kurar ta wuce. *Babban gida* Tunda asuba da sukayi sallah basu kwanta ba, yaran dama duk matasa ne suna iya shirya kansu, dan haka kowa yayi shirin zuwa islamiyya, iyayen ma shirywa sukayi sai Hamna, Amna da Jamila da kuma Umaima, zuwa k'arfe bakwai suka gama kintsawa tare da cika cikinsu, nan fa aka fito dan tafiya gayya guda, masha Allah mota shida sukayi idan aka had'a data tsaron colonel suka cika takwas, a hakan ma wai dan Amar da Ammar da su Junaid sunce sai bayan azahar zasu tafi, motar Jibril aka ce yan matan su shiga, Umaima ce ta shiga gaba tana ta wani basarwa kamar dai Hajia kakarta, Amna ce ta kama murfin mazaunin baya zata bud'e yace "Tsaya." Tsayawa tayi tana kallonshi shi kuma ya lek'o yace wa Umaima "Malama fita ki koma baya akwai mai wannan wurin." Cike da gadara tace "Wa fa?" Had'e fuska yayi yace "Ban sani ba, ki fito na ce ko." Tsaki tayi ta fito saida ta bangaji Amna kafin ta shiga ta rufe tana kallo ta ga wa zai shiga gaba, kallon Amna yayi yace "Shiga nan." Yana fad'a ya shiga ya tayar hakan yasa Amna shiga ita ma ta rufe, sahu ya shiga da motar inda aka bud'e musu k'ofa suka fara fita, Umaima ce tace "Yanzu dan rainin hankali dama Amna ce zata shiga gaba kasa na fito daga nan? Lallai ma yah Jibril ba ka da mutumci wallahi." Juyowa yayi kai tsaye kuma ya kalli gabanshi yace "Qur'ani in ban sauke ki ba kice d'an iska ne ni, ke ni zaki kira marar mutumci, kaji min shegiya kai." 😂😂😂 *Fad'an na yau kuma tsakanin mace da namiji ne* Nuna shi tayi da yatsa tace "Allah kar ka sake sheganta ni, inba haka zan maka tijara a wurin nan, kuma da kake cewa ka sauke ni, ka jima baka sauke nin ba, ko kai baka ga duk motocin dake gabanmu da bayanmu na gidansu ubana bane." Cikin tashin hankali yace "Na gode Allah da yasa akwai motar ubana a ciki, na kuma yi farin ciki daya zama ubana ba matalauci bane bare ace yana zaman kawai ne a gidan na ku, kuma Allah kika sake min magana sai na ci uwarki a cikin motar nan naga abinda zai faru." Hamna dake latsa wayarta cike da damuwa tace "Kai, wallahi wata rayuwar ma batayi ba, ku yanzu da girmanku zaku tsaya kuna wannan musayar yawun haka, a cikin maganganunku fa harda gori kuke son ku shigo da shi, yanzu idan ace iyayenmu suka ji kuna tunanin zasu ji dad'i ne?" Umaima ce tace "Ke bana son iskanci, kar yau dan kun ganni na had'a kafad'a daku yasa kuyi tunanin raina ni, tom." Cikin jin hushi ta ture Jamila dake tsakiyarsu wanda hakan yasa har Hamna saida ta kaiwa glas d'in motar karo, ita ma cike da tsiwa ta bangazo Jamila har ita da ake cutawa tace " A'a kai, ni kuma mena muku? Kunga kuyi fad'an ku amma kar ku saka dani." Suna cikin wannan ture turen Jibril ya juyo yace "Billahil-azim duk wacce naga ta turi yar uwarta saita yabawa aya zak'inta, kunji na fad'a muku." Jin haka yasa suka harari juna sukayi shiru, da wannan kuma suka isa cikin yardar ubangiji, nan dai suma sukayi tasu ta'aziyar, sun samu Hajia kuma ta dire tace da ita zasu koma dan ta gaji da hayaniya da zahi, suna haka colonel ya samu kira na gaggawa a babban birni Niamey, dama tare da mutanenshi yake dan haka ya musu sallama suka d'auki hanya. Bayan sallah azahar kuma saiga Ammar da su Junaid da Amar a mota d'aya, basu wani shiga cikin gida ba nan suka zauna ana ta hira da jimami, bayan sallah la'asar kuma Hajia ta fito cikin shirin tafiya tace gobe ta dawo sai ayi sadakar uku, loiacin Amar suna d'an nesa da gidan dan haka bata ganshi ba, nan aka had'a ta da yan matan da samarin da kuma iyayen maza aka ce su tafi gida tunda babu kowa, saida kowa ya gama shiga aka fahimci Hamna bata shigo ba, saida aka kirata ta fito ashe tana can tana gyara jikinta tana fesa turare, kasancewar Hajia na tsaye ta fito nan ta duba motar da zata shiga sai taga babu wuri, dan haka ta nuna mata motar Ammar data hangeshi shi da Junaid kad'ai, can ta nufa zata shiga baya Junaid ya fito yace "Gimbiya Hamna shigo gaba, ni na ma samu motar da zan shiga." Ita kuma murmushi tayi ta shiga kamar yanda yace, a ranshi kuma cewa yayi "Ba gaira ba dalili na had'a mota da ku kafin mu kai ta kama da wuta, ai wannan tafiyar babbar tafiya ce.". Saida Ammar ya ji motoci na oda alamar sun fara tafiya ya d'ago kanshi, juyawa yayi inda Hamna ke zaune suna had'a ido gabanshi yace wani "Dassss." Ya fad'i ba tare da sanin dalili ba. Inda ita kuma na ta gaban yace "Dammm." Kallon tsoron da take mishi ne yasa ya had'e fuska yace "Dallah ni bari kallo na sai kace mayya." Da sauri ta kalli gabanta a ranta tana fad'in "Toh, aifa kuma na shiga uku, gashi yanzu babu ni babu guduwa idan ma na k'ular da shi." Tashin motar yayi ya fizga da gudu inda ta bi hannunshi da kallo yanda ya murza sitiyarin, k'aramar jakarta ta fito da ita ta d'auki abun sauraro (écouteur) ta danna a kunne saboda tasan zaman shiru ne za ayi, suna shiru haka tana sauraren wak'ok'inta kira ya shigo wayar, d'auka tayi suka fara hira ita da saurayin na ta duk da ba wai son shi take ba, yanda take kashe murya dan kar Ammar yaji yace tayi laifi ashe dai bata tsira ba, dan yanzun ma haushi ne ya kama shi wai akan me zata wani kashe murya haka tana hira da saurayi, cikin hassala ya fizgo wayar hakan yasa abun sauraron ya fita muryar saurayin ta bayyana, yanda shima ya kashe murya ne ya k'ara tunzura Ammar, dan haka saurayin da baisan meke faruwa ba yace "To ai dole ne ko? Yanda kika kashe min jiki haka da muryaki ai sai bacci ya d'auke ni alhalin ina cikin tuk'i." Tsabar neman fita Ammar sai ce mishi yayi "Insha Allahu kana baccin nan ba zaka bud'e ido a ko ina ba sai cikin k'abari, ku ko kunya baku ji ku tsaya hira da 'ya'yan cikinku haka, yanzu haka matarka na can ranta a b'ace amma baka san ya zakayi ka kwantar mata da hankali ba, k'aryar banza kawai." Kashe wayar yayi ya cillata k'asan k'afafun shi inda birki yake yana jan wani tsakin, Hamna dake kallonshi ta kasa gane me yake nufi tace "Yaya Ammmm..." Bai bari ta k'arasa ba ya nuno mata yatsa yace "Kar ki sake ki min magana." Yanda ta ga fuskarshi yasa taja baki tayi shiru, suna tafiya taji shirun yayi yawa, hannu ta zura ta kunna redion motar dan shi tsabar baya son hayaniya ko redio na mota baya kunnawa, tana kunnawa yayi daidai da tashar ana wak'a, cikin jin haushi ya buge hannunta yace "Kar ki sake tab'a komai dake motar nan." Tab'e baki tayi suka ci gaba da tafiya, ana haka ta ji masuburbud'ar sanyi (ac) na bata sanyin dayawa ita kuma bata so, sai kawai ta zura hannu zata d'an juyar da shi gefe, ai kuwa sai ji tayi kanta ya bugu da abun sanyin saboda wani wawan birki da Ammar ya taka, kafin ta ankara taji ya fizgo hijabinta dake jikinta wanda dama ta sanya ne saboda zasu zo wajen rasuwa, kamo hannayenta yayi duka biyun ya had'e wuri d'aya yasa hijabin ya d'aure su tamau, kallonta yayi da jajayen idonshi yace "Kinfi kowa sanin bana magana sau uku akan abu d'aya, nayi biyu ba zaki sani bayi uku ba, idan har na ji bakinki yanzu wallahi bolar dake kan hanyar nan zan tattaro na tusa miki su a baki har sai mun kai gida." Hamna da ido suka cika da hawaye shiru tayi dan babu damar bashi ko da hak'uri ma, bai sake kallonta ba har saida suka isa cikin gari ya kalleta yace "Ke gaki marar kunya, a gabana wani d'an iska zai kira ki har kina kashe mishi murya, shi kuma dayake babban kwarto ne har yana fad'a miki wai zai yi bacci, haba." Hamna dai ko kallonshi batayi ba har suka isa gida, motoci na tsayawa a farfajiyar gida aka firfito, Hamna babu hannayen bud'ewa saida Ammar ya bud'e mata k'ofar ta zuro k'afafu ta fito, take kallo ya koma kanta inda Junaid da dama yasan abinda zai faru kenan ya riga kowa bushewa da dariya, da sauri Amna ta k'araso ta kunce mata hannuwa tana fad'in "Yaya Ammar ne ya d'aure ki? Ke kuwa me kika masa haka kamar wata dabba?" Kamar zatayi kuka tace "Me kuwa zan masa, bak'in halin ne ya motsa da mugunta." Lieutenant ne yace "Yanzu Ammar d'aure yarinyar nan kayi kamar wata dabba, me tayi maka to?" Yana cikin rufe mota ya nufi b'angaren su yana fad'in "Bata jin magana." Cikin b'acin rai lieutenant yace "Kai maganar kake ji? D'an iska kawai yarinya bata maka komai ba ka kamata ka d'aure." Juyowa Ammar yayi ya kalleshi, juyawa yayi ya ci gaba da tafiyarshi haka suma, ana shiga falo Hajia tace "Wai ina shalele na? Ance tare muke amma har yanzu ban ganshi ba." Umaima ce ta tab'e baki a ranta tace "Mu da ba shalelenki ba ma dai gamu ko ba'a san ganinmu." Sai lokacin sukayi ido hud'u da Amar, ai kuwa sakin jakarta tayi ta zaburo ta daddafe fuskarshi tana tambayar "Shalele lafiya? Meya sameka a fuska haka? Ba dai hatsari kayi ba kuma shine babu wanda ya fad'a min." Cikin halin ko in kula yace mata "Eh, ba wani babban abu bane, karki d'aga hankalinki." Hamna ce tace "Amma yaya Amar na d'auka cewa akayi fad'a kukayi kai da yaya Ammar." Da sauri kusan kowa ya kalleta inda Amar har saida yaji kamar ya mareta, Hajia ma kafeta tayi da ido tace "Fad'a kuma? Waya fad'a miki?" Yanda duk taga wasu na kallonta ne yasa tayi shiru, cikin zaro ido Hajia tace "Ba dake nake magana ba kina ji na kinyi shiru." Cikin duburburcewa tace "A'a Hajia nima ban sani ba, jiya dai naji su aunty suna fad'in ko sunyi fad'a ne lokacin da zasu tafiya, amma bansan meya faru ba, mu bamu ma gidan a lokacin." Lieutenant ne ya kalli Amar yace "Amma ai jiya ba haka kuka fad'a mana ba, ka ce hatsari kayi da moto." Hajia ce ta mishi wata tsawa kamar k'aramin yaro tace "Rufe min baki malam, dama ko kun sani wace tsiyar zaku tsinana, duk ba ku kuke d'aure mishi gindin ba." Amar ta kalla tace "Shalele da gaske ne abinda ta fad'a?" Ba tare daya had'a ido da ita ba yace "Ba gaskiya bane, ni banyi fad'a da shi ba." Wani murmushin yak'e Hajia tayi tace "Shalele kasan dai zansan abinda ya faru ko? Ka fad'a min ko kuma na tambayi wanda zai fad'a min komai daya faru." Cike da k'aguwa yace "Hajia ba komai fa, dan Allah abar maganar." Juyawa yayi da nufin komawa d'akin shi yace "Ni zan shiga ciki." Da kallo kawai ta bishi har ya fita daga falon, nan kowa ma ya nufi na shi d'aki dan huta gajiya. Lieutenant na shiga wanka yayi ya sake sabon shiri ya fito, kai tsaye wajen aje motoci ya nufa wanda ke sank'ame da motoci kamar na siyarwa, dan akwai motoci a wurin kusan guda bakwai, a hankan ma dan babu ta colonel sannan Jamil ma moto ne da shi, haka su Hamna ma duk da kuwa akwai halin da zasu hau motar suma, katari akayi Zeituna na share wurin saboda 'ya'yan bishiyoyin dake zuba suna yawon b'ata wurin, duk'e take kusa da motarshi da tsintsiya tana shararta da kuzari kamar yanda ta saba, duk da ba motsin mutum taji ba amma k'amshin turarenshi ya sanar da ita yana tahowa, tana d'agowa ashe ma harya k'araso kusa da ita zai bud'a motarshi, idonsu ne suka had'u wanda hakan ya haifar mata da shiga wani yanayi na shauk'i, shi kuma yana kallonta kai tsaye yayi k'asa da idonshi wanda cikin akasi suka sauka kan k'irjin dake pam-pam a gabanta kamar mai jaririn ciki, gashi dai budurwa har budurwa amma datti ya b'oye hallitunta, yatsina fuska yayi saboda kallon tsaf daya mata, hijabinta kalar ruwan toka ne amma tsabar daud'a har yayi wani duhu, k'afafun nan nata fari k'al da su kamar na mai d'aukar kanwa amma fa daga ciki bak'i k'irin yake, kallon fuskarta ya sakeyi wacce ke fitar da zufa daga goshinta zuwa saman hanci, gashi zufar har cikin kanta zufa yake har tana gangarowa a fuskar, da sauri ya d'auke idonshi ya mayar kan mota ya bud'e zai shiga, cikin ladabi ta sunkuya tace "Abban Ammar a dawo lafiya, Allah ya tsare." Fuskarshi ba yabo ba fallasa ya amsa da "Allah yasa." Tayar da motar yayi tana kallonshi ta kasa ci gaba da aikinta har yayi baya baya ya saita motar daidai k'ofar fita, mai gadi ne ya bud'e masa ya fita duk tana kallo kafin ta ci gaba da shararta. Ashe duk kallon nan da take masa yana hangenta ta madubin motar, saida ya fita yake tunanin wannan kallon duk na miye haka? Ita bata san ba kowa ke son yawon kallo ba? K'aramin tsaki yayi tare da sakin tunanin Zeituna, wayarshi ya d'auka da nufin kiran Ummyn yan biyu saboda ta kira shi yana wanka, kuma yasan ta kira ne taji sun iso lafiya, yana dannawa lambar ta ta ido sai kawai hoton Zeituna da k'irjin ta ya dawo mishi a ido, muryar Ummy ce ta dawo da shi hayyacinshi ya amsa mata sallamar data masa. *Bayan fitar Zeituna* Kawu Mamu na zaune k'ofar gida da redionshi yana saurare wannan mutumin ya zo ya paka mota, fitowa yayi cikin wata arniyar shadda wacce tasa kawu Mamu sanin tabbas babban mai kud'i ne, gaisawa sukayi yace mishi "Baba dama wurinka na zo." Saida ya nuna kanshi yace "Wuri na kuma Alhaji, Allah yasa dai lafiya ko ba wani laifin mukayi ba." Murmushi yayi yace "Babu laifin daka aikata Baba, alkairi ne ke tafe dani." Murmushi ya saki ya mishi izini ya zauna kan tabarmar kusa da shi, ya mik'e yace "Bara na kawo maka ruwa Alhaji." Da sauri ya katse shi da cewa "A'a Baba ka barshi, ai babu k'ishin ruwa a tare dani." Zaune yayi suka sake gaisawa kafin yace "Baba ni dai sunana *Jano*, kuma ni d'an kasuwa ne, a garin nan nake da zama, daren jiya ina kan hanyata ta zuwa gida a kan motona saina had'u da wata budurwa, sanin ba zata tsaya ta sauraren ni ba yasa bai tsayar da ita ba, amma a hankali na dinga biyo bayanta naga ta shiga gidan nan." Ya fad'a yana nuna gidan da suke fuskarta ya ci gaba da cewa "To a gaskiya yarinyar ta kwanta min, ina sonta idan har ka amince da hakan." Kallonshi kawu Mamu yayi yace "Janna ka ke ko?" Murmushi yayi yace "A'a Jano ne Baba." Sake kallonshi yayi yace "Amma dai sunan nan bana musulmi bane ko." Ba fargaba yace "Eh Baba, ni ba musulmi bane, jimawa a cikin musulmi da kuma zama tare da hausawa yasa ba'a iya tantance gaskiyar waye ni, amma ni asalina ma d'an bagwari ne." Gyara zama yayi yace "Wannan ai ba wani abu bane, gaka 'yarmu ka ce kana so kuma mun baka har abada." Kallonshi Jano yayi yace "A'a Baba, bana har abada nake buk'atar ta ba, zan fad'a maka gaskiyar abinda nake so daga jikin yarinyar." 🤔 _Ba aure ya kawoka ba dama?_ *Mu had'e a pegi (page) na gaba insha Allah.* 29/05/2020 à 16:33 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _KUNA CIKIN RAINA_ *Raheenat M. Abbakar* _(My Heenat)_ *Jameela AHK* _(My Meelat)_ *Ma chérie Hakeema* _(Mom Teema)_ *Momyn Dady* *Maman Labyb* *My Hawwer* *Aunty Hawwer* *Ummi&Ummi* _(Lil sister's)_ *Nazeefa* _(My k'awa)_ *Sis Chappa* 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _5_ Bud'ar bakin tsohon sarki cewa yayi "Allah da na shi iko, Imran ai dama ya kamata ka k'ara auren ko dan matsayin da kake da shi, sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba." Cikin nutsuwa Imran ke kallonshi yana kuma sauraro, d'orawa yayi da "Shekarun baya da suka shud'e nayi magana daga ni sai liman akan ina son ya baka auren 'yarsa *Saratu*, amma lokacin daka kawo wacce kake so kuma za'a maka nad'i sai kawai muka bar maganar, a k'a'idata kai ka sani bana sab'a maganata, dan haka har yanzu nake son cika wannan alk'awarin dana yi tsakani na da liman wanda Allah ne shaida." Sunkuyar da kai Imran yayi yana jiran umarnin mahaifin na shi, ci gaba yayi da fad'in "Ka cika min burin nan nawa Imarn ta hanyar had'a zuri'a data liman, tun yaya na (mahaifin Sameera) yana mulki suke tare da shi, amintaccenshi ne, ni ma kuma banda amintacce sama da shi, mutum ne mai rik'on sirri da amana, baya duba matsayinka ko kuma muk'aminka, idan har kayi ba daidai ba take zai sanar da kai ba tare da shakku ba, babu tsoro ko shakkar wani mahaluki a tare da shi inba ubangijin daya halliceshi ba, yaranshi sun samu tarbiya wacce nake da yak'inin zakayi alfahari da auren tsatsonsa." Cike da gamsuwa da bayanin mahaifinshi ya d'ago yace "Mahaifi na wannan hallayar liman ce, dan haka a shirye nake da na bi umarninka." Cikin jin dad'i yayi murmushi yace "Alhamdulillah, ita Saratu yanzu tana gidan mijinta har da ma yaranta, amma akwai k'anwarta wacce akayi wa saukar hardar Qur'ani mai girma satin daya wuce, a lokacin kana k'asar *Paris* shiyasa ma baka samu halartar taron ba, sunan yarinyar *Safiyya*, na yarda da tarbiyarta saboda nasan mahaifiyarta, idan har ka amince da zab'in nan to zanyi magana da liman, amma ka sani, kai ba k'aramin mutum bane da za'a tsaya b'ata lokaci ba." Cikin girmamawa yace "Na amince mahaifina, duk abinda ka zab'a min yana zama alkairi a gare ni, zanyi biyayya ga wannan auren na kuma rik'e yarinyar da daraja fiye da yanda zan kula da kai na." Da haka suka gama tattaunawarsu ya taso ya fito, fadawa biyun ne suka rufa mishi baya izuwa komawa b'angaren shi, yana zuwa ya shiga suka sake tsare bakin k'ofar, d'aya bafaden ne ya kalli d'an uwanshi yace "Zan d'an kewaya, ina zuwa yanzun nan." Da kai kawai ya masa alamar toh kafin ya wuce ya zagaya ta baya, saida ya tabbatar babu mai ganinshi kafin ya sulale ya nufi b'angaren uwar d'aki, cikin sauk'i ya had'u da wata baiwar ta fito daga falonta da wani abu mai kama da k'warya da kayan marmari a ciki, nan ya fad'a mata yana son ganin uwar d'aki, bata b'ata mishi lokaci ba ta juya ta koma ciki ta fad'awa uwar d'akin sak'on dake tafe da ita, tana kishingid'e jakadiyarta na gefe tana matsala mata k'afafu sai lumshe ido take tace "Ki shigo da shi." Mik'ewa tayi cikin ladabi ta nufi k'ofa, a hankali ta bud'a ido ta kalli jakadiyar tace "Ki jira mu a waje, karki bari kowa ya shigo har sai *Kullu* ya fita." Cikin girmamawa da kirari ta mik'e ta fita ta zauna falo shi kuma ya shigo, har saida ya samu wuri ya durk'usa ya gaisheta tare da mata kirarin matar sarki uwar sarki kuma kakar sarki insha Allahu kafin cike da isa da k'asaita tace "Kullu meke tafe da kai a daren nan? Baka san mutanen gidan nan zasu iya saka mana ido ba?" K'ara sunkuyawa yayi yace "Tuba nake ranki shi dad'e, akwai abinda ke shirin faruwa ne a gidan nan da na ga ya kamata ace kinyi gaggawar saninshi." A hankali tace "Me yake faruwa?" "Ranki shi dad'e yanzu haka daga wajen takawa muke tare da mai martaba, sun tattauna sosai, kuma ba akan komai ba sai akan maganar auren mai martaba, takawa yace zaiyi magana da liman kan ya bawa mai martaba auren 'yarsa Safiyya, ya kuma ce ba za'a d'auki lokaci ba." Da sauri ta tashi zaune ta fito da idonta wanda ada take k'ank'ancesu tace "Kuma mai martabar ya amince?" Sake sunkuyawa yayi yace "Ranki shi dad'e sanin kanki ne da wuya takawa ya umarci mai martaba abu kuma ya tsallake baiyi shi ba, sai dai in takawa ne ya janye umarninshi." A harzuk'e tace "Idan kuma bai janye ba fa?" Cikin ladabi yace " Aure zai tabbata ba fashi, tuba nake ranki shi dad'e, Allah ya ja zamaninki, kinyi taki kinyi ta rago." Da k'arfi ta katseshi da fad'in "Ya isa, je ka kawai, ka ci gaba da saka min ido akan duk wani motsin mai martaba, kafin nan zanji da wannan al'amarin." Saida ya mata kirari ya fita daga d'akin ya sake zagayawa ya koma wajen aikinshi, yana fita ta d'auki wayarta ta mik'e tsaye tana dannawa waziri kira, har saida kiran ya tsinke ta sake kira na biyu kafin ya d'auka, cikin hargagi tace "Duk abinda kake gobe ka zo ka same ni zamuyi magana." Cikin girmamawa yace "Uwar d'aki lafiya? Meya faru ne?" "Akwai babbar matsala nake fad'a maka, kawai ka zo ka same ni gobe da safe, kuma bana so ka bari wani ya ga lokacin da zaka shigo nan." "Angama ranki shi dad'e, Allah ya kaimu gobe da safen." Datse kiran kawai tayi ba tace komai ba, jakadiya da ita ma ko da Kullu ya shigo ta biyo bayanshi ta lab'e tana saurarensu, tsaf ita ma ta kwashe komai da suka fad'a ta shirya fad'awa d'aya daga cikin kishiyoyin uwar d'aki mai sunan *Hannatu*. Ta k'ofar da babu mai shigowa sai ita kad'ai tasa makulli ta shigo cikin shigar alfarma ta alkyabba, babu kowa falo kai tsaye tukarar ta wuce ta k'wank'wasa k'ofar, sarki Imran da a lokacin yake kwance kan makeken gadonshi na alfarma yana kallon sama, tunani yake akan abinda ke tunkaro shi, yanda zai fara fad'awa sarauniya Ameera yake tunani, k'wank'wasa k'ofar ne yasa ya kalli k'ofar har saida gabanshi ya d'an fad'i, dan yasan ita ce ta zo, umarnin shiga ya bata ta bud'a ta shigo, zaune ya tashi za zuro k'afarshi daya k'asa ya tankwashe d'aya akan gadon yana kallonta harta k'araso kusa da shi, cikin murmushi da girmamawa tace "Barka da warhaka gwarzona, sarkin Basraba sarkin sarakuna, buhun k'aya kake ba'a cikaka a tausa, kwalli mai sa ido shek'i, d'awisu ne kai ko a dawa namanka sai sarki, na Ameera bada kanka a sare kaje gida ka ce ya fad'i, rugum babban motsi, daji ba'a maka k'aure ko da mahaukacin kafinta, d'an sarki, jikan sarki, kuma uba ga sarkin Basraba da yardar Allah, kaga Abban *Ja'afar* da *Safna*, gaba ka bawa mak'iyanka ba baya ba, da baya ka basu da tuni sun cimma ka, na..." Fizgota yayi ta fad'o kanshi suka fad'a saman gadon suna dariya yana fad'in "Kin gama fasa min kai na yau, ki adana sauran har gobe sarauniyata." Kwance sukayi ya kalli fuskarta yace "Wai ina kike koyon irin wannan sai kace sarauniyar marok'a ta duniya." Murmushi tayi tace "Tun ranar dana auri sarki na shiga makarantar koyon wasa mutum, dan ina so na dinga kod'a mijina." Cikin jin dad'i yace "In kuwa hakane to ya kamata a k'arawa malamin nan albashi, ke kuma miki albishir dana baki kyautar alkyabbata wacce nafi ji da ita." Dafe k'irji tayi cike da murna tace "Wow my King, godiya nake masoyina, Allah yaja zamaninka, Allah ya k'ara maka nisan kwana da lafiya." Da haka suka gudanar da darensu cikin soyayya da k'aunar juna. *Abuja* Rana ta hantse sosai Harira ta zo da yan kayanta, nan Sameera ta gabatar da ita wajen sauran ma'aikatan gidan da kuma Ammie, d'akunan yaran ta nuna mata inda zata dinga kula da shi, fitowa tayi ta barota a d'akin Khalifa da Diya'u tace zata gyara musu duk da Sameera tace ta bari harta huta, tana fita ta juya ta kalli d'akin da kyau, tab'e baki tayi tace "Humm! Sameera kenan, wato yanzu nan ke duk zaman da mukayi tare dake amma ki rasa sakayyar da zaki min sai had'a ni da aikin kula da d'akin yaranki? Ba damuwa, da sannu nima sai nayi iya k'ok'ari na wajen ganin na shigo gidan nan a matsayin kishiyarki, wallahi daga lokacin zata k'are miki." 🙄🤔 *Da abinda kika shigo kenan? To takwara aiki ya samemu ashe, su Harira nasan sai dai in wajensu lamma za'a fara durk'usawa.* Sameera wajen Ammie ta koma ta nemi alfarmar tayi shiru da bakinta kar Abbanta ya sani, dan inhar yasan wacece Harira to akwai matsala, alk'awari Ammie ta mata na ba zai ji ba. *BASRABA* Da sassafe Waziri ya shigo b'angaren uwar d'aki bayan ya tabbatar babu wanda ya ga shigarshi, waya na ga ta ya fiddo a aljihu ya danna camera ya saita wayar a jikin k'ofa ya tangaleta a bayan murfin k'ofar, saida ya kalla ya ga tana hasko mishi inda yake da tabbacin nan uwar d'aki zata zauna sannan yayi murmushi ya shigo, jakadiya na mishi iso ta bar part d'in zuwa na Hannatu dan kai mata tsegumi, a falon uwar d'aki ya zauna yana kallonta fuska a had'e, cikin ladabi yace " Hushi bai dace da uwar sarki ba, uwar d'aki ko zan iya sanin meke faruwa?" Kallonshi tayi tace "Waziri da matsala babba, takawa yana so ya kaini bango har yasa nayi abinda banyi niyya ba." Yana d'an kallonta yace "Ranki shi dad'e lafiya? Me takawa yayi kuma yanzun?" Cikin hushi tace "Na samu labarin takawa yana son had'a sarki aure da yar gidan liman, ni kuma ba zan lamunta ba dan ita ma yarinyar bana k'aunar ta kamar yanda bana k'aunar matarshi Ameera, shiyasa na ce ka zo dan musan abinyi tun wuri kafin lokaci ya k'ure mana." Fuskarshi a had'e shima ya kalleta yace "Yar liman kuma? Amma meyasa takawa zaiyi mana haka?" Shiru tayi sai kumbura da take hakan yasa yace "To shi mai martabar me yace akan lamarin?" A d'an fad'a ta kalleshi tace "Me kuwa zai ce? Ai kafi kowa sanin sarki Imran baya tab'a kaucewa umarnin mahaifinshi, ya amince d'ari bisa d'ari zai aureta, kuma ina tabbatar maka inhar liman da takawa suka had'u yau har suka tattauna, to babu shakka auren sarki da yar liman zai zauna daram, dan ba zasu tab'a jan al'amarin da tsayi ba." Tashin hankali ne k'arara ya bayyana a fuskarshi, shi kad'ai yasan irin k'aunar da yake yiwa mulkin garin basraba, dole sai 'yarshi ta shigo gidan zai cika burinshi, dan haka a shirye yake da yayi komai akan duk wani mai son shiga tsakaninshi da mulkin nan, d'an b'alle botir d'in rigashi yayi da yake jin ya shak'eshi sosai kafin yace "To idan har aurensu ya tabbata ya zamuyi?" A harzuk'e tace "Ba mai zai tabbata ba, kawai kayi wani abu a kai." Wani kallo ya mata mai fassara da dama yace "Kamar me kenan uwar d'aki?" A tsanake ta kalleshi tace "A matsayinka na namiji baka san me zakayi ba da zai hana auren nan? Sai ni ce kake so na samo maka mafita? Bayan kuma 'yarka ce zata shigo gidan, nifa babu wata riba da zan ci, kawai waccen tsinanniyar matar ta shi ce bana son ganinta ita kad'ai a cikin gidan nan." Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta yace "Zanyi duk abinda ya dace a matsayina na namiji, amma ki ban izinin yin komai." Ba tare da tunanin komai ba tace "Kawai ka je kayi koma meye banda matsala da hakan, auren ne kawai bana so ya tabbata." Murmushin gefen labb'a yayi yace "An gama ranki shi dad'e, za ayi komai kamar yanda kika ce." Ganin ta jingina a bayan kujerar yasan ta gama magana kenan, cikin girmamawa yace "Ni zan tafi uwar d'aki, sai kin jini." K'ala ba tace mishi ba har saida ya kai k'ofa tana kallonshi, cikin dubara yayi kamar labulen d'akin ne ya sark'afe shi harya samu ya d'auki wayar ya fice, yana fita ya shigar da d'aukar da yayi ya fara tsare tsaren abinyi. *Da rana* A falonsu Ammie suke zaune bayan sunyi sallah sun ci abinci, suna tsaka da hira téléphone d'in dake kan wani k'aramin teburi dake tsakiyar kujeru yayi k'ara, Rauda ce ta d'auka ta kara a kunne, jim ta d'an yi kafin ta kalli Sameera tace "Ammie kina da bak'o a waje." Juyowa tayi ta kalleta tace "Who is that?" D'auke wayar tayi a kunnenta tace "Saleem, k'anin uncle Abbakar." Da murmushi a fuskarta tace "Ok, ki ce ya barshi ya shigo." A wayar ta sanarwa da mai gadi ya barshi ya shigo, baifi minti biyar ba sai ga Saleem ya shigo da fara'a a fuskarshi, Sameera da murna tace "Saleem, dama kana gari? Kwana biyu ka b'uya." Saida ya k'araso ya zauna kujerar da Jabir ya tashi ya bashi kusa da Abdul yana murmushi yace "Aunty ina nan wallahi, abubuwa ne sai a hankali." Murmushi tayi tace "Good, ina Abbakar da jiki kuma?" Saida yanayin fuskarshi ya canja kafin yace "Jikinshi da sauk'i." Hannu ya bawa Abdul suka gaisa da Jabir, har Khalifa da Usman ma, Diya'u ne ya taso yana turo baki yace "Ni baka gaisa dani ba, dan ban girma ba ne?" Dariya Saleem yayi ya bashi hannun yana fad'in "Sorry my Man, ai kai ma babba." Khalifa ne yace "Kaji yaron da ko gemu bai fara ba zai ce ba'a gaisa da shi ba." Ammie ce ta rik'e baki tace "Ikon Allah Khalifa, to kuma ita gaisuwar dole sai mutum yayi gemu?" Imranatu ce tace "To Ammie ki fara tambayarshi ma shi ina nashi yake?" Cike da kuri Khalifa yace "Ai naga man da Dadyna yake anfani da shi gemunshi na k'ara yawa, da nace zan shafa yace na bari zai soyo min wanda suka fi na shi zama original." Juyawa Sameera tayi saida ta kalli duk ' yan matan d'akin tace "Yanzu dukaninku babu mai wayon da zata kawowa bak'o ruwa? Yaushe kuka zama marowata haka?" Raihan ce tayi saurin mik'ewa saboda shakkar uwar da take tana fad'in "Sorry Ammie." Da harara ta bita harta shiga kitchen d'in su Ammie ta d'auko ruwa da lemu har kala uku, tunda ta tashi Saleem ya bi bayanta da kallo, a ranshi yace "Tabbas ke ce *target* d'ina." Su Bilkis ne suka ce mishi sannu dan shi ba niyyar gaishe da su yake ba saboda hankalinshi baya nan, cike da kunya ya gaishesu har Raihan ta dawo ta dire farantin gabanshi, tunda ya d'ora idonshi a kanta ya kasa d'aukewa, har ta zuba mishi lemun ta mik'a mishi ta mik'e ta koma inda take ta zauna yana kallonta, Fadila ce ta lura da kallon dan haka a ranta taji ita da zai so Raihan d'in ma ya taimaka mata saita samu Abdul ita kad'ai, yana d'an kurb'a lemun ya aje ya mik'e yace zai tafi, godiya Sameera ta masa tace ya gaishe da Abbakar da jiki, kuma insha Allahu zataje ta duboshi dan ta jima rabonta da can, Abdul ne ya mik'e ya d'an taka mishi har k'ofar gida ya shiga motarshi kafin ya bar unguwar. Yana fita wayar Sameera tayi k'ara, d'auka tayi ta duba sunan taga sarki Imran ne, d'auka tayi tana murmushi da zolaya tace "Allah ya taimaki sarkin Basraba, k'anena ya kake?" D'aga b'angaren Imran ne yace "Yarinyar nan fa kin gama raina ni, shekara uku na baki amma har kike kirana da k'aninki." Cikin dariya tace "Amma dai kasan k'anwata kake aure ko?" Saida ya kalli Ameera wacce ke mik'o mishi smootie d'in ayaba yace "And so what? Ni kuma yayanki ne." Cikin dariya tace "To ya garin na ka mai martaba?" Imran ne yace "Muguwa, ban sani ba to, kina son sanin yanda garin yake da aka ce za'a baki mulkinshi kika ce ba kya so? Gashi kinsa duk an takura ni ta ko ina." Tunda ya fara magana take dariya saida ya tsaya tace " Ai na fad'a muku ba zan iya mulki ba, amma ko yanzu bata b'ace ba ai, idan ka samu labarin wata masarautar zata kawowa taku hari to kayi gaggawar sanar dani dan mu shirya dakaru ni kuma zan jagoranci yak'in." Murmushi Imran yayi yace "Ke 'yar bala'i ko? To bama fatan tashin hankali mu. Kafin tace wani abu yace "Ina mamana take da yarana?" Saida ta kalli Ammie tace "Duka lafiyarsu k'alau, ina yaran nawa da yar uwata?" Katseta yayi da fad'in "Dakata dallah ki saurare ni, serious magana fa na kiraki muyi." Mik'ewa tayi daga wurin ta shiga bedroom d'in Ammie ta zauna bakin gado tace "What's the matter?" Nan ya kwashe komai ya fad'a mata duk yanda ake ciki kafin ya d'ora da "Yanzu haka ban fad'awa Umma ba, dan nasan halinta ba wani farin ciki zatayi da zab'in na takawa ba, haka ma sistern ki ban san ta yanda zan fara fad'a mata ba, please Sam tell me what do i do now, wallahi i'm confuse." Dariya Sameera tayi tace "Hey! What trouble in this issue? Listen to me brother, maganar nan babu wata matsala ko tashin hankali, ka samu aunty ka fad'a mata komai dake faruwa, sannan ka jira abinda uncle da liman zasu tattauna, idan har maganar ta fad'a shine saika samu Ameera ka fad'a mata, i hope zata fahimce ka d'ari bisa d'ari." Ajiyar zuciya ya sauke yana hangen Ameera dake gyaran kayanshi yace "Ok, yanzu zanyi abinda kika ce, but make me sure k'anwarki ba zata d'aga min hankali ba." Dariya tayi tace "I'm verry sure, kai dallah rago wallahi ka cika tsoro, kamar dai ba jinin *Ali zaki (Haidar)*." Wata sayayyar ajiyar zuciya ya sake saukewa yace "Babu abinda ke kayar min da gaba a duniyar nan kamar idonki dana Ameera, sometimes bana iya kallon k'wayar idonku na fad'a muku abinda ke raina." Tashi tayi zata fito tace "Matsoraci, u know me ai tha's why u scrad me." Daga inda yake yace "God forbid na ji tsoronki, kema duk iskancin ki ai kina shakkar wannan yaron." Zaro ido tayi tace "La la la la, mijin nawa ne yaro? Kai amma sarkin nan baka da mutumci aradu, amma ba komai kai da yallab'ai ne, zai sameka har Basraba dan kayi repeatn abinda ka fad'a." Yasan tsaf Abbas zai titsiyeshi kan ya maimaita kamar yanda tace, shiyasa yace "In dai kina k'aunar iyayenmu karki fad'a masa, abinda ma a daren nan jirgi na zai tashi zuwa Belgium (ya fad'i hakane dan tayi tunanin zai bar garin)." Dariya tayi tace "Fad'uwa ta zo daidai da seat kenan, ai shi tuni ya rigaka isa can." Da sauri yace "No wonder yau mukayi magana dake perfect, banji yana ta min iskanci ba ko yana shinshinarki yana kissing d'inki ba, ashe jarababben baya gari." Dariya tayi harta fito suna ci gaba da raharsu, cikin zolaya yace "Dallah ni bani uwata na kwashi albarka." Saida ta k'araso kusan Ammie tace "What are u eaten na baka na following down? Gata in dai Ammie duk tsiyarka zaka bar min abata." Ammie ta ba wayar suka gaisa harda su Imranatu ma da sauran yaran kafin daga bisani suyi sallama. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Sai dare kad'ai Imran ya samu uwar d'aki ya fad'a mata abinda suka tattauna da takawa, ranta ya kai k'ololuwa wajen b'aci, ace d'an ta kuma babban d'anta wai ba zai iya fara sirri da ita ba, ba yabo ba fallasa ta nuna mishi ai ba komai kawai Allah yasa alkairi, dan tasan waziri zai lalata komai, shi kuma mamaki ne ya sa shi mik'ewa da k'yar ya mata sallama. *Me waziri zaiyi? Wa sarki zai aura? Me zai samu takawa?* _See u.✋_ 03/06/2020 à 23:33 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _7_ "Dan Allah baiwar Allah ki tsaya, zo ki shiga mota saina kaiki duk inda zaki je." Kasa had'a ido tayi da shi sai lumshe ido take kamar jiri zai deb'eta, jin ba tace komai ba sai k'ok'arin tafiya da take yasa ya sake tareta yace "Ki dubi girman Allah baiwar Allah ki saurare ni, ki zo na kaiki asibitin, zan taimakawa mahaifinki ya samu lafiya, karki d'auki abinda ya faru yanzun da son raina nima wall..." Bai k'arasa saboda tafiya data fara yi, ji take kamar ta watsa mishi mari ko guda goma ne ko ta huce, amma kuma tsoronshi take ji, karta mareshi ranshi ya b'ace ya sake murk'usheta a wajen, dan ta fahimci sunyi hannun riga da imani, sake wucewa tayi ko kallonshi ba tayi ba bare ta saurare shi, shi kuma tausayin yarinyar ne ya kama shi sosai, juyawa yayi yana kallonta tana tafiya da k'yar waacce ya gani cikin karsashi wani lokaci daya wuce, wata zuciyar ce ta fad'a mishi "To me kenan kayi Jibril? Ka lalata rayuwar yarinyar daka had'u da ita yanzun nan? Yarinyar da ko sunanta baka sani ba, shin baka tunanin sanadiyar abinda ya faru ta rasa mijin aure? Ba ma wannan ba Jibril, shin kasan me zai iya biyowa baya sakamakon hakan? Kai tirr da wannan rayuwa taka." Da gudu ya sake tare gabanta kamar zai rik'e ta saboda yanda ya bud'e hannayenshi a dole tareta zaiyi yana fad'in "Kinga baiwar Allah, dan Allah ki zo muje mota sai mu tafi tare, na amince ki kaini wajen iyayenki na taimaka miki, idan har mahaifinki ya samu lafiya na miki alk'awarin zan aure ki, ki zo muje dan Allah." Wani kallo ta watso mishi dake nuna me ka d'auke ni? Amma ba tayi magana ba ta sake giftawa zata wuce, hijabinta ya rik'e tana juyowa suka had'a ido, ruwan dake sauka da k'arfi ne suka fara tsagaitawa a hankali, cikin raunin murya yace "Idan ba zaki aminta da ni ba dan Allah ki fad'a min sunanki da gidanku, zan zo, zan zo wajen iyayenki na nemi izinin aurenki." Wasu hawayen takaici ne taji sun taho mata bata shirya ba, wai yau ita ce wani namiji da bata san shi ba kuma akan hanya ya mata fyad'e, kamar a film ko kuma tatsuniya, ko kuma kamar ana rayuwa a garin maguzawa, da k'arfi ta bige hannunshi ta sake juyawa tayi tafiyarta, baya da zab'in daya wuce ya shiga motarshi ya tayar ya bi bayanta, ba jimawa suka isa asibitin, tana zuwa a k'ofar d'akin da mahaifinta ke kwance ta samu duk dangi an fito sai sharar hawaye suke, mahaifiyarta da ke kuka sosai ta matsa kusanta tana tambayar lafiya, shirun da kowa ya mata ya tabbatar mata da mahaifinta ya rasu, Mari na gamsuwa da abinda zuciyarta ta fad'a mata sai lokacin ta ji wani azababben kuka na bak'in cikin mutuwar mahaifinta da abinda ya faru da ita yanzun, durk'ushewa tayi wajen ta fashe da kuka sosai kamar ranta zai fita, nan dangi har da kakarta suka dinga rarrashinta suna bata hak'uri, amma Mari ta zama kamar dutsi ko jinsu ba tayi sai kuka kawai, duk abin nan dake faruwa a idon Jibril dake hangensu daga nesa, lura da abinda ke faruwa yasa ya k'ara jin ba dad'i sosai, gyara tsayuwa yayi da niyyar ko zai kwana nan sai ya ga gidansu, amma rashin sa'a sai kiran gaggawa ya shigo wayarshi cewa ana nemanshi, dan a lokacin bai jima da fara aiki da wannan projetn ba, kawunshi Gambo ya shiga gaba har saida ya ga ya samu wannan aikin, dan haka baya da zab'in daya wuce ya shiga motar ya bar wajen. Ko da ya isa inda suka sauka ya d'auka kira ne na ka zo yanzu ka koma, ashe a lokacin wani abu ne ya taso da dole za'a tura su wani garin, kuma shine zai wakilci tawagar, haka suka kama hanya zuciyarshi kamar zata fashe, ya rasa meke mishi dad'i a rayuwa, kamar ya fasa ihu yake ji ko zaiji sauk'in abinda ke ranshi. Nan gawar mahaifinta ta kwana zuwa safe aka yi bisarshi, har lokacin Mari kuka take ga azabar ciwon kai da zazzab'i da suka tasota gaba, ta k'i ci ta k'i shan komai sai kuka kawai, kowa kuma tunanin shi kukan mutuwar mahaifinta ne dan haka sai dai ace kiyi hak'uri mana, duk mai rai mamaci ne, addu'ar ki yake buk'ata ba kuka ba, a kwana a tashi sai gashi sun kwashe *sati d'aya*, a ranar wanda suke haya gidanshi ya zo yace sai dai su tashi ya samu wanda zai zuba a gidanshi, dama kuma bashi ne a kansu sosai, da k'yar wani mak'wabcinsu ya bashi hak'uri yace shi zai dinga biyan kud'i har zuwa lokacin da mahaifiyarta zata gama takaba, dan d'akinta ya dace tayi wanka. Haka suka ci gaba da rayuwa tare da kakar Mari a gidan, basu da matsalar abinci saboda lokacin zaman makoki an kawo musu, har lokacin kuma Mari ta k'i sakin jikinta, duk wani motsi da zata yi sai taga kamar suna kallonta kuma zasu fahimci abinda ya faru, dan haka kullum da hijabi a cikin gida, mahaifiyarta kuma tuni ta kafa mata na mujiya tana bin dindigin kowane motsinta dan tasan ba haka take ba, kwatsam sai aka kwashe *wata uku har da kwana sha biyar* Mari babu al'ada, abinda ya kusa tarwatsa zuciyar mahaifiyar ta. Ta fito daga ban d'aki da hijabinta da bokiti a hannu mahaifiyar take kallonta tayi wani fes sai d'aukar ido take, cikin kallon nan tace "Zo nan Mari." A hankali ta aje bokitin ta k'araso kusanta ta tsaya, hannu ta zura da nufin kama nata hannun ta duk'ar da ita sai kawai Mari da babu gaskiya ta zille, kallon mamaki ta mata tace "Meye? Mari kar dai abinda nake tunani ne ke shirin faruwa dake?" Cije leb'e Mari tayi tuni ta fara sharar k'walla tana fik'i-fik'i da ido, dafe k'irji *D'iyar baba* (sunan da suke kiranta dashi kenan kasancewarta 'yar fari kuma kakanta ne yayi rainon ta) tace "Na shiga uku na lalace, Mari iskanci kike dama? Yaushe kika lalace ban sani ba?" Da sauri ta girgiza kai sai rufe baki take da hijabi, cikin jin haushi D'iyar baba ta taso ta shak'o hijabin Mari, ita kam ana jawota saita fad'i k'asa ta fashe da kuka tana fad'in "Wallahi Ayya banyi ba, ba laifina bane, ki tsaya na fad'a miki abinda ya faru, shi ne fa ranar kawwww..." Marin da D'iyar baba ta watsa mata yasa ta dafe kunci ta kwamtsa k'ara, kafin ta sake cewa wani abu D'iyar baba ta d'auki kujerar data mik'e a kai 'yar tsugunno ta maka mata a kai, wannan azababbiyar k'arar da tayi tasa kakarta dake shigowa saurin d'aga k'afa ta ida shigowa tana sallallami da tambayar kai lafiya? Ganin wacce ake jibga yasa ta zubar da ledar hannunta ta k'arasa ta rik'e ta cikin harshensu na barebari tana fad'in "Ke dube min yarinya, me tayi miki? Kamar kin samu jaka." D'agowa D'iyar baba tayi ta nuna Mari cikin son d'aukewar numfashi tana fad'in "A..a...a..ta cu..ceni, cikin...sh..eg..e..." Zubewa tayi wajen sumammiya, ai fa sai wani tashin hankalin ya samu kuma, take bakinta ya karkace saboda hawan jinin da take fama dashi, amma duk da haka nuna Mari take tana fad'in "Allah ya isa...Allah ya miki abinda kika min...bani ba ke Mari har abada." Duk da maganarta ba'a jin sosai amma Mari ta fahimci me take fad'a, ai kawai sai kakarta ta kifa mata wani marin ta fara masifa ita ma wai zata kashe mata 'ya har tana fad'in "Wallahi idan 'yata ta mutu dalilinki kema sai kin mutu, da ubanki *Muhammadu* yana raye kikayi wannan abun kunyar da shima ya tsine miki albarka". _Masu karatu karfa ku manta babu kirkira a ciki, duk abinda ya faru ne da wasu mutanen nake rubutawa bayan an bani labarin._ Wannan yammaci Mari bata kwana gidansu ba, domin kuwa D'iyar baba tace ita ba yarta bace , kakarta kuma da zasu tafi asibiti saida ta watsowa Mari kayanta sannan ta rufe gidan, a daren nan duk inda Mari take tunanin samun taimako na yan uwa saida taje, amma da sunga yanayinta suka tambayeta lafiya ta k'i fad'a sai wasu suce ta koma gida zasu zo su ji meya faru sai a sasanta, har gidan *malam Rabi'u* taje a tunanin kamar kaka yake gareta saboda da shi da kakanta wanda ya haifi mahaifinsu uwa d'aya uba d'aya suke, sa'a da ta ci shine baya gari kasancewarshi malami ne na tsibbu, shiyasa ta baro gidan da tunanin da yana nan daya karb'e ta tunda malami ne shi. A tak'aice dai Mari a gindin wata bishiya ta zauna ta rakub'e, kuka take da tunani barkatai na yanda lokaci d'aya komai ya canza mata, mahaifiyarta ta kasa tsayawa ta saurareta, yanzu ya zatayi kenan? Meye abunyi? Ina zata je? Wannan tambayoyin ta dinga jerawa kanya kafin daga bisani zuciyarta ta fad'a mata ta je gidan k'anwar mahaifinta *Khadi*, ta san matar kuma tana nuna mata soyayya saboda Maryama sunan mahaifiyarsu ne aka saka mata, ko rasuwar mahaifinta saida ta so ta tafi da ita amma dai ta jinkirta har wani lokacin, matsalar d'aya ita ce ba garin nan take ba, tana Maradi ne da aure, amma a yanda zuciyar Mari ke tafasa dole ta shirya ta kuma k'udira gari ya waye ta tafi can duk da bata da kud'in mota, a haka kuwa aka fara kiran sallah asuba, tashi tayi daga wurin ta samu wani masallaci tayi alwala da butar nan, gefe ta koma tayi sallah kafin ta d'auki hanyar zuwa gidan mota. A k'ofar shiga gidan ta fara rarraba ido tunda ita dai ba kud'in mota gareta, haka ta shiga ciki tana ta zagaye ta rasa abunyi, tana ji kamar ta rok'i wani amma tana jin tsoron k'ara neman taimako, tana haka wani matashi da gani kasan d'an makaranta ne dake shirin tafiya hutu wani garin ya mata magana, a tak'aice dai shi ya taimaka mata ya biya mata kud'in motar bayan ta fad'a mishi bata da kowa anan tana so taje gida ne, tare suka zauna kujera d'aya matashin nan duk inda aka tsaya saiya siye abu ya bata, duk da tana tsoron sakewa da shi har saida ta d'an saki jiki, kallonshi tayi tace "Dan Allah me sunanka? Sai tafiya muke har yanzu baka fad'a min ba." Kallonta yayi yana murmushi yace "Ke ma ai baki fad'a min ba, kawai kince min kinyi b'atan kai ne shiyasa ni kuma zan taimaka miki." Tayi tace "Sunana *Maryama*, amma wasu na kirana da Mari." Murmushi ya mata shima yace "Ni kuma *Issa*." Da haka suka d'an dinga hira kafin Allah ya kaisu lafiya, suna sauka ya nemi lambar wayarta tace bata da, ya nemi kwatancen gidan tace bata san ya zatayi ta kwatanta mishi ita ma dan ta jima rabonta da garin, ya yarda da hakan dan ko harshenta bai gama fad'awa a hausar ba, taxi suka shigo tare har aka ajeta k'ofar gidan tanti Khadi wacce labarin abinda ya faru ya riga Mari isowa wajenta, hakan kuma ya faru ne lokacin da Mari taje gidan wata yar uwarsu, bayan tafiyarta hankalinta bai kwanta ba saita kira kakar Mari, cikin hushi ta fad'a mata wai Mari cikin shege ta musu dan tozarci, yanda abun ya daketa ne yasa ta kasa hak'ura ta kira Khadi tana tambayarta wai hakane? Ita kuma sai lokacin taji meke faruwa, ita ma dai kusan sumar tayi, amma daga baya haka ta dinga fad'a tana masifa wai Mari ta zubar musu da mutumci, su a zuri'ar su kaf babu wanda ya tab'a cikin shege sai ita, har ta wayi gari tana wannan kwakwazon, abun bai bar tunaninta ba kuma sai ga sallamar mari ta diro garin daf da magrib, tunda ta k'ura mata ido bata d'auke ba har mari ta tsargu, yan uwa in dai kaiku in baro Khadi ma bata karb'i Mari ba, cewa tayi sam ba da ita ba kawai ta koma wajen uwarta data d'aure mata gindi (duk da ta ji uwar fa suma tayi), duk magiyar duniya ba wacce bata mata ba amma ta rufe ido, har saida tace mata "Ki gode Allah da kawu *Rabi'u* baya gari abin nan ya faru, ba dan haka ba da har kasheki zai iya yi, dan shi baya lamuntar wannan iskancin." Sai lokacin Mari ta fahimci dalilin da yasa bata samu malam Rabi'u ba, kenan da yana nan da abun ya munana?haka ta fito da kunyar ganin bak'on data tsayar da niyyar ta shiga ta kawo mishi ruwa tantin ta kuma ta mishi godiya na alkairin daya mata, haka suka jera ita da shi basu san ina zasu je ba, shi dai ba zai iya tafiya da ita gidan da ya zo hutu ba, to meye abunyi, har aka gama sallah magrib suna tafiya kafin Mari shed'an ya zugata tace saurayin ya bata lambarshi zata kirashi idan taje wani wurin, rubuta mata yayi yana kallo harta b'ace ma ganinshi, doguwar tafiya tayi har ta zo wucewa ta ranpoint d'in hôpital, anan ne suka fara had'uwa da Iklima, kallon farko da Iklima ta mata sai ta ji tausayinta saboda tana tafe tana kuka da yake nuna k'unci a tare da ita, tsayar da ita tayi suka gaisa ta tambayeta ko lafiya? Da farko kasa fad'a mata komai tayi, amma sai Iklima ta mata karamci ta hanyar zuwa da ita gidan da suke zaune ita da sauran yan mata masu yawa, sauran abinci ta bata ta ci sannan tace ta saki jikinta, cikin fargaba ta kwashe komai ta fad'a mata abinda ya faru da ita, tab'e baki Iklima tayi tace ... "Ai matsalar iyayenmu kenan, zaki shekara dubu kina kare mutumcinki, amma rana d'aya idan tsautsayi ya fad'a miki ki kayi ciki to sun manta, nima abinda ya faru dani kenan, sai dai ni da amincewata na yarda da saurayin saboda ina son shi, shigar rabo yasa na samu ciki, amma haka suka fara min horon yunwa ga tsanani ko kulani basa yi a gidan, ça tsangwama da hanta ta yayyu na, shiyasa ni kuma da naga yunwa na neman halakani na bar musu gidan, yanzu nan nake rayuwata duk da mahaifiyata na so na koma gidan yanzu, kuma cikin dana fito da shi ina haihuwarshi na kaiwa ubanshi, ni kuma na ci gaba da neman kud'i na." Da mamaki Mari ta kalleta tace "Kenan ke ba korarki sukayi ba? Amma me yasa ba zaki koma ba tunda suna so ki koma? Sannan meye sana'ar da kike anan d'in?" Duk wata tambaya da Mari ta mata saida ta bata amsar ta, amma sai Mari ta k'yamaci abun ta nuna ba zata iya ba, dan haka Iklima tace "To idan kina ganin yanzu a duniyar nan ana taimako dan Allah ki fita ki jaraba nema ki gani, mace dai ba zata iya miki taimakon da a yanzu kike buk'ata ba sai namiji, to ki jaraba neman taimakon mazan ki gani idan basu miki kallon sama da k'asa ba." Mik'ewa tayi zata fita tace "Ki samu ruwa kiyi wanka, idan kin gama ki rufe min k'ofar d'akin dan ba ni kad'ai ke zaune ciki ba, idan har baki samu taimakon ba zaki iya dawowa ki same ni tunda kinga inda nake." Da kallo ta bita harta fita, tana fita ita ma ta d'auki jakar kayanta ta fito ta kama hanya, ina zata je? Wa zata nema taimako? Abinda ya sameta dalilin neman taimakon ne fa, tana cikin tafiyar ta tsaya bakin titi kamar wacce zata tsallaka amma tunaninta ba nan yake ba, tana haka kuwa wani matashin saurayi da alama irin yaran nan ne masu jiran shago ya mata magana, maganar ma bata alkairi ba saita banza, wai a nawa zata siyar zai biya? Jin haka saita tsorata ta dawo baya gidan Iklima, a gurguje dai nan suka had'e suka fara wannan rayuwa ta k'ask'anci, kamar yanda Mari tace ita k'aramar karuwa ce, domin kuwa duk kud'in da zata samu basa wuce na yan buk'atu abin ci abin sha yar sutura marar tsada, ciki kuma na girma tana rainonshi tare da tunanin irin tarbiyar da zata bawa wannan cikin idan ya fito, saida cikinta ya tsufa ta daina fita sai Iklima kad'ai, a wannan lokacin sai take jin Iklima kamar yer uwa da suka fito ciki d'aya, tana haihuwa ma Iklima ce tsaye kan komai kamar ita akawa haihuwar, har akayi suna sai dai *Nurul Huda* bata samun gatan da aka yanka mata rago ba har yau maganar da ake tana shekara shida da haihuwa, bayan haihuwarta tayi arba'in suka ci gaba daga inda suka tsaya, bata sake waiwayar gida ba bare tasan meke faruwa, sai dai tana had'uwa da yayan Khadi a cikin gari har ma su gaisa, lokacin da suka samu kud'i ne sai suka kama gidan hanya wanda duk matan aure ne a gidan, mace d'aya suke abin arzik'i da ita maman Husna, ita ma bata nuna musu tsana ko kyara shiyasa, ana haka Junaid ya ganta wajen bikin wani abokinshi sunje d'aukar abinci gidansu k'awar amaryar wacce ita ta asassa taron suna tsakiyar fili suna rawa, ita ba abokiyar ango bace bare kuma amarya, kawai mawak'in ne mutuminsu shine ya gayyace su kuma suka je, dama kuma in zasuje irin wannan shiri ake na musamman, dan ko rigar nono basa sakawa bare wando saboda ana so komai yasan an motsa shi, haka kawai yarinyar ta mishi yaji ta birge shi, ya kasa gajiya da kallonta, daga ranar ne fa yake bibiyar rayuwarta kuma har yanzu bai daina ba duk da yasan wacece ita, tak'aitaccen labarin Maryama kenan. *Ci gaban labari* Ya jinjina sosai da jin labarin, shirun da yayi yana tunani barkatai yasa Iklima mik'ewa tace "Na tafi ni saida safe." Bai iya kallonta ba har ta wuce, da k'yar shima ya tashi ya shiga motarshi sai dai babu kuzari a tare da shi, gida ya nufa cike da k'warin gwiwar jin wani hukunci daya yanke yana daf da isa gidan. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Tun yamma Hamna ke son amsar wayarta a hannun Ammar amma ta rasa yanda zatayi, har saida akayi sallah isha'i sannan ta shirya cikin shiga irin ta Amna sak ta nufi b'angaren na samari, tana isa bakin k'ofar ta tsaya tana k'wank'wasawa tare da yin sallama, Ammar da ke zaune falo shi kad'ai yana latsa wayarshi sai wayar Hamna aje gefenshi, a hankali ya d'ago kai ya sauke kan k'ofar, take kuma ya mayar da kallonshi kan wayarshi duk da dai muryar da Hamna keyi tayi sak data Amna, saida ya d'auki kusan minti biyar bai sake d'agowa ba kafin yace "Shigo." A hakan ma ba tare daya kalli k'ofar ba. Cikin nutsuwa kamar yanda tasan yer uwarta nayi ta shigo tana sake wata sallamar, bai amsa ba bai kuma kalleta ba har ta tsaya tsakiyar falon, a sanin data mishi yasa bata tsaya b'ata lokaci ba ta fara bayani kamar haka "Yaya Ammar, dama zan kira Mamanmu ne a wayar Hamna saboda tawa babu kati a ciki, sai tace wayar tana hannunka kuma kaga idan akayi sallah isha'i ba'a barinmu fita ko yara bare..." Wannan bayani da take jin shi yake kamar saukan ruwan sama da k'ank'ara a tsakiyar kanshi, k'aguwa tasa ya d'auko wayar dan dama ta ishe shi saboda wayan kiran da ake ya mik'o mata, hannu ta zuro ta karb'a tace "Nagode." Sai lokacin kad'ai idonshi suka kalli na ta idon, gabanshi ne yaji ya fad'i da sauri ya d'auke idonshi daga kanta, juyawa tayi zata fita a lokacin kuma Jibril ya shigo falon da kular abinci a hannunshi, saida ta kusa kaiwa k'ofa ta juyo ta kece da dariya tace "Allah sarki boss, a hakane kake cewa kana son zama soja bayan baka iya gane waye wannan waye wannan, to kai fa ina ganin ko namiji ya zo maka a shigar mace saika yarda." Tunda ta fara magana yake hasosho irin muguntar da zai mata, hakan yasa shi kallon Jibril da suka fi kusa cikin kaushin murya yace "Wallahi kai zai ci wa uwa idan har baka rik'e min ita ba." Tsuru Jibril yayi ya juya ya kalli Hamna data tattare zanin atamfarta, to shi taya ma zai fara rik'e ta ne? Juyowa yayi ya kalli Ammar daya had'e fuskar nan kamar hadarin gabas, sai kawai ya juya da sauri ya nufi k'ofa, Hamna na ganin haka ta rufa a guje da tunanin ita zai kama, shi kuma yasan sai Ammar ya cuce shi, tunda kuma ba zai iya kamota ba gwara ya bar masa gidan, da kallo duka ya bisu kafin yayi k'wafa yace " *Kankana* kenan, zaki shigo hannu na ne, zaki gane shayi ruwa ne."Jibril kam k'ofar gidan ya zauna a teburin mai gadi yana cin abincin suna 'yar hira. Iyayen na zaune a falo suna hira k'asa kasa saboda Hajia na d'aki kar a dameta, wayar Zeinabu ce tayi k'ara tana neman agaji, d'auka tayi ta duba mai kiran hakan yasa gabanta tsinkewa ya fad'i, datse kiran tayi kafin ta mik'e tace tana zuwa ta shiga d'akin ta, maida kiran tayi da sauri kuwa aka d'auka ana fad'in "Eh lallai Zeinabu kin cika 'yar halak, yanzu har ni zan dinga kiranki amma kina kashewa? To yayi kyau, ni dama ba wani abu yasa na kiraki ba na kira ne inji ya ake ciki? Wata kusan biyu kenan ba sak'onki bana mijinki, shine nake so naji ina aka kwana?" Har yanzu gabanta bai bar fad'uwa ba a haka ta amsa mata murya k'asa k'asa da " *Inna* Dan Allah kiyi hak'uri, wallahi bana shareki bane, abubuwa ne suka min yawa, colonel kuma nasan ba wai bai nemeki bane aiki ne dai yasha kanshi, amma kiyi hak'uri insha Allahu gobe zan aika miki da kud'in wata d'aya kafin colonel ya dawo." Da k'arfi tsohuwar tace "Duba Zeinabu, kinfi kowa sanin bana son ana min wasa da maganar kud'i, ki tabbatar gobe kin aiko min kud'in da zanyi cefanai dasu dan kayan abinci na sun k'are, sannan ba zan iya tsayawa jiran mijinki ba, ki kirashi a waya ki fad'a masa ya aiko min da sak'on kamar yanda mukayi yarjejeniya da ku, idan kuma ba haka ba wallahi wallahi *asiri zai tonu*, ehe!" Da sauri tace "A'a Inna ba sai anyi haka ba, insha Allahu zan tura miki nawa sak'on gobe nan, yanzu ma dan dare yayi ne, colonel kuma zan kirashi yanzu na tuna mishi dan nasan sha'afa yayi." Cike da gadara tsohuwar tace "To, kashe waya." Cikin sanyin jiki Zeinabu ta datse kiran ta sake kiran lambar colonel, yana ganin lambar ta yayi murmushin da ba kowa zai iya gane murmushi yayi ba ya d'auka, cikin wani irin amon murya da ba zaka fahimci yanayin da mai ita ke ciki ba yace "Ai na d'auka ba zaki kirani ba, ashe dai ina da rana ta." "Ni ba abinda yasa na kiraka kenan ba, na kira ne na fad'a maka Inna ta kirani yanzu, bansan dalilin daya hanaka cika alk'awarin daka d'auka ba a wannan watan da har ta kira ni take k'ok'arin tayar min da hankali." Daga b'angaren shi ya amsa da "Kin kira ne kenan dan ki min fad'a ko me? Saboda ke ce uwata zaki tsareni kina fad'a min maganar nan." Ita ma a hassale tace "Amma ai kasan kai ka d'auki alk'awari ko? Dan haka dole ka cika." "Idan na k'i fa? Dukana zakiyi? Wai ko dan kinga bana kusanki ne zaki nemi ki min iskanci?" Murmushi tayi kamar a gabanshi tace "Ba ma zaka yarda ba wallahi, tunda ka fara dole ka kai k'arshe tunda laifinka ne koma menene." Wai, colonel Hussein da yake ji kamar ya ganta gabanshi ne ya harzuk'o yace "Laifi na? Laifi na ma kike cewa? A waccen ranar ni nace kiyi abinda zai tayar min da hankali? Ko kuma tursasaki nayi? Ba da amincewarki komai ya faru ba?" K'asa tayi da ta ta muryar tace "Duk da ba tursasani kayi ba ai ba kana nemana na amince maka ba, sannan bani na ce ka kirani inda kake ba, da kuma na zo kaga zan tayar maka da hankali me ya sa ba kayi gaggawar korata daga wajenka ba?" D'orawa tayi da "Duk kai ka ja mana wallahi, ba dan kasa tsoron Hajia a ranka ba da yanzu muna rayuwa cikin salama, amma tsoron wanda baida wutar da zai samu ya saka mu sai aikata laifi muke akan wani laifin." Rintse ido tayi saboda jin k'arar ya bugi wani abu da yake nuna mata da ita ce a kusa da ita ya kaiwa wannan haura, datse hak'oran shi yayi ya rasa bakin magana, ina ma zai ji an kawo masa hari ta baya ko ya samu damar huce wannan haushin, jin baiyi magana yasa tace "Ni duk ba wannan ba, kayi azamar turawa Inna kud'in ta kamar yanda kukayi da ita, dan ni dai ba zan so asiri na dana yarona ya tonu ba a wannan lokacin, gaskiyar magana kenan." "Kutumar bala'i." Inji colonel a cikin zuciyarshi dan har yanzu ya kasa sakin hak'oran shi, "Wannan ma ai raini ne, Zeinabu umarni ne take bani ko me? Ni? Ni? Ina!" Buga wayar yayi a bango ta baje tare da kai wa bangon naushi, Zeinabu dai ta fad'i abinda ke ranta ta kashe waya ta dawo falo. Jibril ne a d'akin kakarshi bayan ya gama cin abinci suna hira, kallonta yayi da fara'a a fuskarshi yace "Yar tsohuwa, insha Allahu idan aure na da Amna ya tashi da kaina zan tuk'aki ki kaini wajen dangi Baba, dan wallahi ina so na gansu sosai." Tunda yayi maganar nan ta had'e fuska tayi shiru, jin shirun yasa yace "Hajia, wai a wane gari dangin mahaifin Baba suke? Na gaji da tambayar Umma akan wannan." Ba alamar wasa ta kalleshi tace "Kenan ni ce yanzu zaka dama? Malam tashi ka fitar min daga d'aki." Da mamaki ya kalleta yace "Hajia, kema damuwar ce kamar yanda Umma ke damuwa a duk sanda na mata magana makamanciyar wannan?" Cikin d'aga murya tace "Ban sani ba Jibril, kuma in har baka son gayyato fushina to kayi gaggawar janye wannan k'udirin naka na son ganin dangin mahaifin mahaifinka." Mik'ewa yayi da tsantsar mamaki yace "Saboda me? Meyasa Hajia baku so ana..." "Na ce ka fita." Ta fad'a da k'arfin gaske, juyawa yayi jiki a sanyaye ya fita yana tunanin meke faruwa, fitowa yayi k'ofar gidan da tunanin shiga motarshi daya bari anan, Junaid ya had'u da shi zai shigo hakan yasa ya tsaya ya fito suka gaisa, Jibril ne yace "Na ga yau sai wani farin ciki kake mutumina, ko dai Maryama ta amince ne?" Wani murmushin ya sake yi yace "Bata amince ba, amma dai na gano hanyar da zanbi nasa ta amince." "Wace hanya kenan?" Ya tambaya da zumud'i, da murmushin gefen labb'a yace " *Zan je garinsu, sannan na shirya tsakaninta da mahaifiyarta da sauran danginta."* Da fara'a Jibril yace "Eh to kuma fa ka zo da dubara, kana shirya tsakaninsu zaka ga ta amince kosu su amince da kai." Kallonshi yayi yace "Amma dai zaku rakani ko?" Zaro ido yayi yace " Ni da wa?" Hararanshi yayi yace "Kai da zaratan 'yan uwa na mana." "Har da Ammar?" Cewar Jibril, ba wasa yace "Har da shi mana, ai watak'ila ma ya mana anfani fiye da kai, dan in mukayi sa'a muka had'u da wani tsagera a cikin dangin mai taurin kai shi zai mana maganinshi." Juyawa Jibril yayi zai nufi motarshi yana fad'in "Shikenan to sai kuje babu ni." Da sauri ya rik'o shi yana dariya yace "Kai haba daga wasa, kai fa zaka nuna mana hanyar ma tunda ai kasan hanyar *Gouré*." Cak ya tsaya ya juyo yana kallon Junaid, Goure, wannan yarinyar? Tana nan har yanzu? A ina take? Ina zanje na sameta? Rik'e hannun Junaid yayi yace "Da gaske kake? Yaushe zamu tafi?" "Eh to, ni ko gobe ma zan iya tafiya, amma ka bari mu fara jin ta bakin su Ammar da Amar." Hannunshi ya kama zuwa cikin gidan yana fad'in "Muje ciki muyi magana da Ammar yana nan, Amar idan ya shigo zamu fad'a mishi kuma kasan ba matsala zai bamu ba." Wucewa sukayi ciki Junaid na fad'in "Wai duk wannan saurin na miye haka? Kamar wanda zaije ganin tashi budurwar." Wani murmushi Jibril yayi, dan haka kawai ya ji kamar ana fizgarshi da yaje garin, yana so ya Allah ya sake had'a shi da yarinyar nan, suna zuwa suka saka Ammar tsakiyarsu Junaid ne yace "Babban yayanmu, dama wata alfarma muka zo nema, dama yarinyar nan da nake so ce ta fad'a min garinsu, to akwai yar matsala tsakaninta da iyayenta, shine nayi shirin tafiya neman aurenta wajensu tare da shirya tsakaninsu, to bana so ne naje ni kad'ai gaskiya, nafi so muje tare da ku dan su san ni d'an dangi ne." Ammar da hankalinshi ke kan waya saida yaji ya kai aya kamar mai ciwon haure yace "Ina da abinyi." Yana fad'a kuma ya mik'e ya shiga d'akin shi, Junaid ma ya mik'e yana tab'e baki sai ga Amar ya shigo, nan suka fad'a mishi kuma kamar yanda suka sani dama ba zai basu matsala ba, shirya yanda tafiyar zata kasance sukayi kafin kowa ya nufi d'akin shi. *Zanyi magana, amma ba yanzu ba.* 03/06/2020 à 23:33 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _6_ Ma'arufa ce da Ma'aruf a d'aki kowa da wayarshi yana dannawa, kwance take akan katifa mai tufun gaske shi kuma tashi katifar bata da maraba da bargo, kallonta yayi yace "Ke wai kin fara shirin tafiyar ne gobe ko kuma kina nan kina jan jikin?" Ba tare data kalleshi ba tace "Ba gobe zan tafi ba." Ba tare daya daina kallonta ba yace "Saboda me?" Kai tsaye tace "Saboda akwai wasu kud'i da Labo zai bani gobe idan ya zo, kuma ina so na shiga kasuwa na siyo sabbin yadin da za'a min sabbin riguna dogaye, tunda waccen gurguwar tace mutumin ba wai harkar matan banza yake ba." Tsaki yayi yace "Ke dan Allah kiyi duk iskancin da zakiyi zuwa jibi ki bar garin nan, na k'osa kud'in nan si shigo wallahi harka ta bud'e, dubi shegiyar katifar da nake kwana akai." Sai lokacin ta kalleshi tace "Wai kai yanzu ko kunya baka ji? Kana kwance gida ni ce zanje na nemo maka kud'in da zaka ji dad'in rayuwarka da su." Ba tare da damuwa ba yace "To meye a ciki? Ke ma sau nawa ina miki anfani? Yanzu lokacinki ne yayi." Tsaki taja ta mayar da kallonta kan wayarta tace "K'aton banza kawai." Kallonta yayi amma bai biye mata ba saboda yana wata hira data d'auke mishi hankali, wata budurwarshi ce mai sunan *Meena* ke ikrarin daina harka dashi tunda baya sonta baya kashe mata kud'i, maida mata sak'on yayi da "Rabuwa dani a daidai wannan gab'ar na nufin ke asararriya ce." Maido masa tayi da "Sai dai in kaine asararren, shege d'an iska wace tsiyar kake tsinana min?" Shima mayar mata yayi da "Ke haba matsalata dake banza ce, kanki baya kawo wuta ko kad'an, ina nufin idan kika barni a wannan lokacin to zakiyi asarar wata opportunity da muka samu." "Ban gane ba d'an rainin hankali, fahimtar dani?" Nan ya fad'a mata wai sun samu wani Alhaji gara zasu wanke shi, kuma k'ashin bayan tafiyar abokiyarshi ce Ma'arufa, dan haka karta bari damar nan ta wuce ta, nan dai suka sulhunta komai ya wuce. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Yanda Abbas yayi tunanin aikin zai kaishi kwana uku sai ya zo da sauk'i, dan haka ya shirya ya taho ba tare daya fad'awa madame ba, su a lokacinsu dare ne dan har sun shiga bacci, saida ya fara shiga wajensu Ammie da suma har sun kwanta ya gaishe su, daga nan kuma part d'in shi ya wuce ya aje jakarshi yayi wanka, kayan bacci ya saka ya feshe jikinshi da turare mai sanyin gaske kafin ya d'auki makullin k'ofar da zata sada shi da falon Sameera ba sai ya fito ta farfajiyar gidan ba, yana shiga ya tabbatar sun jima da kwantawa, d'akin Raihan ya fara bud'a k'ofar a hankali ya lek'a, saida ya sauke ajiyar zuciya sabida ganin tana bacci hankali kwance, duk da har yanzu bai siya mata waya ba amma dai yana tsoron sharrin zamani da dubarar 'ya'yan yanzu, rufewa yayi ya lek'a d'akin Rauda, Khalifa da sauran yaran, amma yana ganin Abdul raheem shi kad'ai kwance a gadonshi babu Ameer ya tabbatar yana wurin mamanshi, a hankali ya shiga can cak ya tsaya, rarraba ido yakeyi tare da shafar kai, a hankali ya fara takowa har ya zo kusa da ita ya tsaya, jefar da makullayen yayi kan gado ya bud'e mata hannayenshi yace "Come on my angel, i miss u." Sameera da tunda mota ta shigo gidan ta farka a hankali cikin turo baki ta bud'e hannayenta ta kwanta luf a k'irjin shi, lumshe ido yayi ya sauke wata ajiyar zuciya mai d'an k'arfi wacce iska da gumin bakinshi har suka sauka kan fuskarta, k'ara shiga jikinshi tayi tana sake matseshi sosai saboda k'aunar mijin nata, ido rufe take sauke ajiyar zuciya tana shak'ar turarenshi dake son mayar da ita bacci, cikin muryar shagwab'a tace "Me yasa baka fad'a min zaka zo ba?" Saida ya fara yawo da hannayenshi a gadon bayanta yana latsawa saboda taushi da laushi ba tare daya bud'a ido ba yace "I'm sorry, nima bansan aikin zai sakeni yau ba, ina k'arasawa kuma naji ba zan iya kwana nesa da ke ba, shiyasa na garzayo na zo gareki." K'ara daidaita zamanta tayi cikin k'irjinshi shi kuma yana sake matseta yana shafata, cikin wata murya mai kama data bacci yace "Meerata." "Uhmmm." Ta fad'a ba tare data kalleshi ba, d'orawa yayi da "Zan samu kulawarki a wannan daren kuwa? Naga baba na yayi kane-kane a kan gadon." D'agowa tayi ta kalleshi ta juya ta kalli Ameer dake ta baccinshi, sake kallonshi tayi tace "Ka d'auke shi mana saika kaishi d'akin su." Kallon Ameer yayi shi ma ya zagaya zai d'auke shi yace "Allah kasa kar yaron nan ya hanani sakewa." Murmushi tayi wanda harya fitar da sauti, kallonta yayi yace "Wallahi yaron nan rigimarki ce ya koya, ko da yana jariri bai hanani yin rayuwa da ke ba kamar yanda yanzun yake hana ni." Zaune tayi bakin gadon tace "Watak'ila yana tsanani buk'atar a kasance auta ne shiyasa, yasan idan ya baka fili saika masa k'ane." Harara ya cillo mata yace "Idan na tashi yi a hanani na gani, kinsan dai ko gabanshi na so zanyi yanda nake so ko?" Dariya tayi tace "To ka barshi yanzu saimu jaraba mu gani." A lokacin daya d'auki Ameer ne yace "Bana so na jefo shi k'asa ai." K'arar bud'a k'ofa yasa Ameer bud'a ido tare da zabura ya kalli wanda ya d'auke shi dan ya hango mamanshi zaune, rintse ido Abbas yayi wanda yasa Ameer cikin muryar bacci cewa "Yeee! Dady na ganka bud'e idon." Kafin ya bud'e idon ido ya sake cewa "Dady yaushe ka dawo? Ka kawo min computer ta?" D'ago shi yayi suka kalli juna yace "Muje na kaika d'akinka ka kwanta da safe zan nuna maka wacce na siyo maka, ko Khalifa baya da irinta." Ai sai Ameer ya dirko daga kafad'ar Abbas yace "Um um Dady, ni tare da Ammie na zan kwana, abinda ma tunda ka tafi tare muke kwana, kai kaje d'akin ka." Da gudu ya yo kan Sameera ya kwanta kan cinyoyinta yana kallon Abbas, ganin yana nufoshi yana fad'in "In dai kana son na baka computer sai ka zo mun tafi, idan ba haka ba kuma sai dai na bawa *Amjad* (d'an Naseer) ita." Zagaya hannayenshi yayi ta kunkumin Sameera ya mak'aleta sosai yace "Um um, bana so ni dai." Dariya Sameera tayi rumgume shi tace "Babana kenan, yaro kwana a gado d'aya tare da mahaifiyarshi yafi mishi komai na duniya ko?" "Eh Ammie." Kwance Abbas yayi kan gadon dan ko yace ya zare mishi ido kuka ne zai saka musu a daren nan, kallonshi yayi yace "Zo nan baba na nayi kewarka sosai." Rarrafawa yayi ya kwanta kan k'irjin shi ya rumgume shi, Sameera ma kwance tayi ta d'ora kanta a kafad'ar shi tace "Ka ci abinci kuwa?" Ido lumshe yace "Um." Tsautsayi yasa Sameera cewa "Auta na kayi abinci kaji, kasan..." Wata k'ara ta saki saboda mintsinin da Abbas ya mata a mazaunai, zaune ta tashi idonta har sun fara ja saboda zafi, kallonshi tayi shi kuma ba tare daya kalleta ba yace "Gobe ma na sake jin kin kira shi auta kiga yanda zanyi da ke." Kamar zata fashe da kuka tace "To meye a ciki dan na kira shi da auta dan Allah?" Ido rufe kamar wanda zaiyi bacci yana ci gaba da shafa bayan Ameer yace "Saboda yawon kiran na shi da auta zaisa wata rana ki fad'a lokacin amsar addu'a, ni kuma so nake sai kin dire min sha biyu insha Allahu." Shiru ta mishi ta kwanta, gashinta yake shafawa da d'aya hannun a haka har bacci ya d'auke su. *BASRABA* Tunda garin Allah ya waye Takawa yake jin kamar ba shi ba, a haka har akayi sallah la'asar ya dawo b'angaren shi kan kilisarshi ya kishigid'a, haka kawai yaji yana buk'atar ganin liman, dan haka yasa d'aya daga cikin masu tsaron k'ofar shi ya nemo mishi liman, kusan dama unguwar duk duk fadawan fada ne a ciki, dan haka ba jimawa sai gashi ya dawo tare da liman, jakadiyar uwar d'aki na ganin haka ta garzaya ta fad'awa uwar d'aki, cikin tashin hankali tace "Kin tabbatar liman ne ya shiga wajenshi?" Cikin girmamawa tace "Ko zanyi k'arya uwar d'aki harshena yayi kad'an daya furta miki k'arya, yanda na ga liman tare da bafaden nan ina fatan ganin annabi haka." Wata ajiyar zuciya ta sauke marar dad'in sauti tace "Tashi kije, amma kar kiyi nisa dan zan buk'ace ki." Tashi tayi ta fita ita kuma ta d'auki waya ta kira waziri, yana danna ok ya sake danna wurin nad'ar duk maganar da zasuyi kafin yayi magana, cikin tashin hankali tace "Waziri ka ce na bar komai a hannunka, amma gashi kana neman ka mana kwance da aiki, ko kasan cewa takawa ya nemi ganin liman? Yanzu haka suka turakarshi." "What!" Cewar waziri, sausauta murya yayi yace "Ki gafarce ni uwar d'aki, yau ba sai gobe ba zan miki maganin matsalar nan." "Ka tabbatar?" "Na baki tabbacin haka." D'if ta kashe wayar, sai lokacin kuma ta tambayi kanta "Amma me yasa baki tambayeshi meye zaiyi ba?" Shiru tayi tana tunani kafin daga bisani ta d'aga kafad'a irin bai dameta ba tare da cewa "Koma me zaiyi indai zaisa a fasa auren kuma naga yarinyar can Ameera cikin garari to hakan ya isheni." A wajen takawa da liman kuma sun jima suna tattaunawa kafin ya mishi maganar neman auren Safiyya, nan liman ya nuna mishi ba komai ya kuma gamsu da bayanan takawa, amma duk da haka saida yace idan har akwai matsala to gwara abar maganar, takawa ya nuna mishi babu komai kawai suyi musu fatan alkairi, da haka takawa ya nemi alfarmar a d'aura auren nan kusa, amma liman yace a bashi lokaci dan sanar da mahaifiyar yarinyar da ita yarinyar kanta, cikin mutumta juna suka gama tattaunawarsu liman ya bar takawa lafiya. Bayan tafiyar liman haka kawai takawa ya nemi ganin duka iyalin na shi a turakarshi, nan suka hallara uwaye da 'ya'ya maza da mata, nasiha ya dinga musu da gargad'i da jan kunne akan rayuwa, daga bisani ya musu addu'a tare da jadadda musu rik'o da zumunci, kar su yarda su bari mulki ko abin duniya ya shiga tsakaninsu, da haka kowa ya tashi ya koma inda ya fito suka bar takawa lafiya k'alau. Wannan ganin shine na k'arshe da suka mishi da numfashi a tare da shi, domin kuwa waziri ne ya biya wasu yan daba guda biyu sukayi shiga irinta fadawan gidan aka shigo dasu gidan a motar dreba ta kai yara makaranta, wajen takawa suka shiga suka taushe mishi kai da pillow har saida ya daina numfashi, tunda asuba kuma aka farga da rasuwar takawar, liman daya zo masallaci da k'arfin gwiwar sanar dashi kowa ya amince, kuma bayan nan yayi istikhara kan lamarin, duk da ubangiji ya nuna mishi wani duhu a cikin abun amma kuma hasken dake ciki shi yafi yawa, dan haka ya zo da niyyar idan sun gama sallah ya fad'a mishi ya amince ko juma'ar da zata zo ma za'a iya d'aura auren ba damuwa. *Abuja* Tunda asuba da sukayi sallah sukayi karatu suke zaune falo cikin raha da k'aunar juna, Abbas ne ya kalli Raihan yace "Mama na wai har yanzu sakamakon na ku bai fito bane?" Cikin sakin fuska tace "Dady yau zai fito, anjima kad'an zamu je mu dubo." Kallon Abdul yayi yace "Abdul, anjima ka shirya zamu fita tare da kai a motarka." Da girmamawa ya amsa da "Ok Dady, zuwa k'arfe nawa?" Kallonshi Abbas yayi yasan ya tambaya ne dan ya shirya kafin lokacin, dan haka yace mishi " 08:00 pm." Jinjina kai yayi yace "Ok Dady." Cike da kunya Raihan ta kalle shi tace "Dady, alk'awarin mu?" Da mamaki yace " Wane alk'awari kuma nayi mama na?" Sanda kanta tayi k'asa cikin kunya tace "Dady u promise me zaka fitar damu abroad idan result d'in mu yayi kyau." Murmushi yayi yace "To banda rigimar mama na ai result d'in bai fito ba, ki jira ya fito sai mu gani." Cikin sangarta tace "Dady gaskiya mun fasa zuwa abroad d'in, mu *Niger* muke so mu tafi." Murmushi yayi kafin yace wani abu Ammie dake zaune tace "Shawara mai kyau, kinga kenan lokaci yayi da zaku kaiwa auntynku ziyara." Rauda ce da sauri tace "Wace auntynmu kuma?" Hararanta Ammie tayi tace "Husna da zatayi aure niger ba dalilin auntynku dake aure a can bane ita ma harta samu miji a can." Cikin yanayin na tuno Rauda tace "Ohhh hakane fa, ki ce aunty *Khairiya* ('yar Bakura yaya ga Husna), gaskiya indai hakane aunty Raihan zanje tare da ke nima na ga niger." Cikin ruwan sanyi Raihan tace "Babu inda zaki bini yarinya, ki jira idan auren Husna ya tashi saiku tafi tare da Ammie." Abbas ne yace "To ai ko ke baza ki ba sai auren ya tashi, in ya so daga basraba saiku wuce niger d'in." Turo baki tayi tace "Amma dai Dady za'a baro ni can wurin aunty Khairiya ko?" Mik'ewa yayi yana fad'in "U have a choice." Ganin ya nufi kitchen yasa Khalifa cewa "Dady kayi b'atan kai, nan fa madafa ce." Juyowa yayi yace "Wajen matata zanje, dukanku nan kun manta da ita tana can tana faman girka mana abinda zamu ci." Dariya Khalifa yayi ya d'ago mishi yatsa irin 👍yace "Fatan alkairi Dady, amma fa banda fad'a kuma, kar ku zo ku rikice mana sai munje rabo." Dariya Abbas yayi ya mishi dak'uwa yana fad'in "Hancin ubanka Imran." Yana bud'a k'ofar kitchen d'in Harira ce ya fara hangowa suna ta kai da kawowa, wani bak'in ciki ne yaji ya taso mishi tare da tuna abubuwan da suka faru a baya, k'aramin tsaki yayi ya juya zai fita sai kuma Sameera ta juyo, murmushi ta sakar masa ta mik'awa Razeena had'in kabejin da tayi tace "Ki saka a fridge kafin a kammala sauran." Karb'a tayi ita kuma ta juya wajenshi tana ci gaba da murmushi harta isa tana fad'in "Barka yallab'ai, har kun kammala karatun?" Hannunta kawai ya kama ya nufi wajen cin abinci da ita, Harira na ganin haka cikin dubara ta aje aikinta ta bi bayansu, dan dama ana aikin banda hararan Sameera babu abinda take tana ayyanawa a ranta wai ita ce mai bayar da oda a duk fad'in gidan nan, lab'ewa tayi tana jin me suke fad'a, Abbas ne cikin rashin son magana yace "Sam, dan Allah me zai hana ki sallami yarinyar can? Idan taimakonta kike so kiyi why not ki bata kud'i tayi sa'a, amma dai ta bar gidan." Da mamaki tace "Why? Me tayi kuma yanzu?" K'ura mata ido yayi yace "Tambayata ma kike? Kinga, ina so ne nasan zaki iya sallamarta ko kuwa?" D'an had'e fuska tayi ta turo d'an bakinta gaba tace "Please sir forget about Harira, mun riga da mun gama maganar nan fa, kuma fa ni bance kai zaka biyata kud'in albashinta ba, so dan Allah ka manta kawai." Wani kallo ne ya mata baki bud'e sai yayi kamar zai girgiza kai sai kuma ya fasa, wai Sameera ce ke fad'a mishi ai ba shi zai biya mai aiki ba, sai lokacin ya girgiza kanshi tare da sakin mamakin dake kan fuskarshi yasa hannu ya shafi yalwataccen gemunshi yace "Ok, duk abinda kikayi d'aya ne, amma ki sani duk abinda zaije ya dawo babu ruwa na ni." Da k'arfi ya fara takawa da nufin tafiya b'angaren shi, da sauri ta rik'e hannunshi a lokacin kuma Harira dake lab'e harta koma kitchen, kafeta yayi da ido fuska ba annuri, ita kam cikin kwarkwasa tace "Do something now, ka samu kayi wanka kafin ka fito na had'a maka break a part d'in ka, dan bana son yara ma su dameka." Fizge hannunshi yayi yana fad'in "Sai me? Ina ruwanki idan sun dame nin?" Juyawa yayi zai fice ta bishi da murmushi tana fad'in "Kayi wankan fa, yanzun nan zan kawo maka break d'in." Juyowa yayi harda dafe k'ugu yace "Mayunwaci ne ni? Kinga yunwa a jikina ne?" Gimtse dariyarta tayi ta girgiza mishi kai alamar a'a, saida ya sake juyawa tace "Allah dai ya huce zuciyar mijina." Cak ya tsaya ba tare daya juyo ba, wato ta mayar dashi wani shagirigirbau, sake rik'e k'ugun shi yayi ya juyo yana kallon cikin idonta ya nunata da yatsa yace "Billahil-azeem idan ban b'arar dake ba ki ce d'an iska ne ni." Tintsirewa tayi da dariya abinda ya k'ara bashi haushi kenan, da gudu ta nufi falo inda tasan Ammie na nan, da k'arfi ta shiga falon tana dariya tana juyawa taga ko ya taho, shi kuma a sukwane ya taho yana kawowa falon ya fara tafiya a hankali, Khalifa na ganinsu yace "Yeah, anzo gurin." Duk da kujerar da Ammie ke zaune ta zaman mutum d'aya ce amma bai hana Sameera zaune a k'afafun Ammie ba ta d'ora kanta a k'irji kamar wata beby tana fad'in "Ammie kin ganshi ko." Ammie kuma dan taya b'era b'ari saida ta fara shafa bayanta kafin ta harari Abbas dake kallon Sameera tace "Kai kuma meye haka da sanyin safiya zaka taso min 'ya gaba da gudu? Wallahi fa bana son abin nan da kake min, yarinya ko babu laifin bak'i bana fari saika dinga cutar min 'ya." Abbas kallon ikon Allah yake, hakan yasa Sameera yi mishi gwalo tana dariya, Abba ne ya kallesu yace "Wallahi wata rana saita karya miki k'afafu, kuma a k'arshe yaro na za'a bari da kashin kud'i wajen neman magani." Ammie ce tace "To idan bai kashe na shi kud'in ba ai muma muna da kud'in kashewar, sannan shi kud'i zai kashe auta ta kuma jinyata zatayi." Saida Sameera ta sake cukuikuyeta tace "K'warai kuwa Ammie na." Wata jar harara Abba ya jefa mata wacce tasa ta mik'ewa daga k'afafun Ammie bata shirya ba, dan har yanzu akwai wutar bala'i a jikin mahaifinta wacce ta ninka ta ta sau dubu, tsaf ta fahimci me hararan daya mata ke nufi, shiyasa ma ta mik'e tayi shiru, juyawa Abbas yayi zai bar falon yana fad'in "Allah ya shiryaki." Muryar Abba ce ta dakatar dashi da yaji yace "Liman kuma? A wannan lokacin." Juyowa yayi ya ga Abba ya mik'e ya nufi k'ofar fita yana d'aukar kiran da liman ya mishi, bayan sun gaisa ne Abbas yayi saurin tambayar lafiya? Dan haka kawai ba zai kirashi ba a wannan lokacin, cike da muryar jimami liman yace "Yallab'ai sai dai hak'uri, kamar yanda muka sani ne kowane mai rai lokacinshi yake jira, to a daren jiya Allahn daya bamu takawa ya fimu son shi ya kuma karb'i abinshi, sai hak'uri kawai." Duk da Abba bai zubar da hawaye ba, domin kuwa mutuwar mahaifiyarsu da kuma ta mahaifiyar Sameera *(Khadija)* ne kad'ai ya zubar da hawaye, amma hakan ya girgiza shi sosai, cikin sanyi jiki da maimaita kalmar inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un ya shigo falon, suna ta hayaniyarsu, wajen Ammie ya nufa inda Abbas ya bi bayanshi ya tsaya saboda ganin yanayinshi, saida ya kalli Sameera da Abbas da Ammie kafin yace "Ku shirya, tafiya basraba ya kama mu yanzun nan." Sameera da gabanta ya fad'i ne tace " Abba, lafiya? Meya faru a basraba?" Ko kallonta baiyi ba dan haka Ammie ta mik'e tace "Yallab'ai lafiya? Meya faru ne? Ko wani ne ya rasu?" A hankali ya jinjina mata kai alamar eh, Abbas ne yayi saurin cewa "Abba waya rasu?" Saida ya had'e yawun da suka bushe mishi a mak'oshi kafin ya kalleshi, kamar ba zaiyi magana ba saboda yanda ya kafeshi da ido, can kuma sai yace "D'an uwa na, d'an uwana da shi kad'ai ya rage min, *Musayyib* ne ya rasu daren jiya." Yana fad'a ya juya a sukwane ya bar falon alamar yana son b'oye yanayinshi, Sameera da ko da aka fad'i haka ta tuna da kiran daya mata jiya bayan sallah isha'i yana sake mata nasiha data dinga hak'uri da rayuwa, bayan haka har suka tab'a hira yana fad'a mata ya nemawa d'an uwanta auren 'yar liman, sun jima suna waya amma yanzu ace babu shi, neman durk'ushewa tayi hakan yasa Abbas saurin tallabota ya rumgume a jikinshi, tana jinta a k'irjin shi saita fashe da kuka sosai tana cakumar rigarshi tana k'ara sautin kukan, Ammie da ba zata iya hanata kuka a wannan lokacin ba dan tasan yanda suke da kawunta, soyayyar da yake nuna mata ko mahaifinta baya nuna mata ita, fita tayi ita ma dan suyi shirin tafiyar, yaran na ganin haka suka mik'e kowa ya nufi d'akin shi zuciya cunkushe saboda ganin mahaifiyarsu na kuka, Raihan saida ta rik'o hannun Sameera cikin rawar murya tace "Dan Allah Ammie kiyi shiru ki daina kuka, takawa addu'arki yake buk'ata yanzun, shine soyayyar da zaki nuna masa." D'akinta ta haura ita ma sai Abbas daya nufi da Sameera b'angaren shi yana rarrashi, ita kuma sai fad'a masa take jiya fa ya kirata sun jima suna magana, yanzu ace wai ya rasu, a ciwon komai da komai, yana shiga d'akin shi ya zaunar da ita bakin gado ya d'auki wayarshi, Bashir ya kira ya fad'a masa, Bashir da a lokacin ke zaune falo yana sauraren hayaniyar yara Imranatu kuma da Ma'awa da ke ta k'ok'arin shirya abun kari, kallonta yayi baiwar Allah tana cikin farin ciki, taya zai fara fad'a mata rasuwar mahaifinta, ajiyar zuciya ya sauke ya mik'e ya tunkareta, hannunta ya kama har zuwa d'akin kwanansu kafin ya fara mata da nasiha sannan ya rarrasheta, yana fad'a mata ita ma ta fashe da kuka ta fad'a saman k'afafun shi, haka dai ya lallab'a ya taimaka mata ta shirya dan Abbas yace yanzu zasu tafi, wajensu Bilkis da Naseer ma haka abun yake, inda Abbas bayan ya gama waya dasu ya kira captain Ali ya sanar dashi zasu tafi basraba. Cikin k'ank'anin lokaci kowa ya gama shirinsa ya fito, Sameera kitchen ta nufa ta samu Razeena ta fad'a mata su kula da gida sosai, sannan tace wa Harira ta kula da yaran, a wannan lokacin da Sameera a cikin nutsuwa take data fahimci kallon da Harira ta mata na kin ma raina min hankali ne, haka suka fito sun kuma samu driver har ya zo d'aukar yaran zuwa islamiyya, saida suka ga tafiyar yaran kafin suma Abbas ya jasu a d'aya motar kuma Naseer ne, suna isa airport captain ya riga daya iso, ba b'ata lokaci suka shiga kowa ya kimtsa suka d'aga sai masarautar basraba. Da saukarsu mota uku ce sarki Imran ya turo dan d'aukar su, masha Allah, unguwar cike take da mutane da ababen hawansu, rasuwa ce data jijjiga masauratar dama kewayenta gaba d'aya, jimamin da mutanen gidan ke ciki yasa tsohon sarki mahaifin Sameera da ma ita kanta Sameera da kuma yar sarki mai mutuwa Imranatu basu samu gaisuwa da irin wasasun da ake ba idan sun zo, k'arfe *08:30* motoci sukayi gudan layi mai tsayin gaske zuwa mak'abarta. *Allah ka mana kyakyawan k'arshe.* *Muje da sauri*: Abba ne ya bayar da umarnin ayi addu'ar uku har ta arba'in ma, domin kuwa irin mutanen da suka halarci jana'izar bai kamata ace sai sun sake dawowa ba, dan har masarautun dake kewayensu ma sun hallara, take aka had'a akayi addu'ar amma hakan baisa jama'a barin gidan sarautar ba, kamar da wasa sai gashi har anyi *kwana biyu* da rasuwar sarki mai murabus, a wannan kwanakin kuma uwar d'aki hankalinta ya tashi sosai, tunaninta ya karkata kan wane irin banzan mataki ne waziri ya d'auka akan mijinta? Me yasa bai fad'a mata irin wannan matakin zai d'auka ba? Da tayi gaggawar dakatar da shi, har yanzu tana so ta keb'e dashi dan suyi magana, amma rashin gaskiya yasa duk wani motsinta sai taga kamar wani yana kallonta, dole ta hak'ura da tunanin idan anyi uku kowa ya watse zata neme shi. *Yau kwana uku*, Sameera dama jiya gidansu kawu Bakura ta kwana tare da mijinta, hakan yasa yanzun sukayi sammakon shigowa masarautar dan shirya komawa, tun farfajiyar gida bayi ke durk'usawa suna gaisheta tana amsawa, ita da Abbas b'angaren uwar d'aki suka nufa dan tunaninsu kowa na can, amma suna daf da kaiwa sai jakadiyar uwar d'aki *Lami* ta taho a sukwane ta sunkuya tana wasata tare da fad'a mata ana mata magana a falon mai rasuwa takawa, juya akalarsu sukayi zuwa can, suna shiga tare da sallama suka samu taron jama'a, uwar d'aki, mahaifinta da mahaifiyar Abbas, waziri da matarshi ga kuma liman da sarki Imran, gefe ma dai duk su Naseer ne da su Imranatu, wuri suka samu suka zauna kusa da juna, Abba ne yayi gyaran murya ya kalli liman yace "Liman jiya munyi wata magana da kai akan auren Imran da kuma yar wajenka, hakane?" Cikin jinjina kai liman yace "Hakane." Imran ya kalla yace "Imran, kasan da maganar nan ko kuwa?" Cikin ladabi yace "Na sani Baffa." Kallon mutanen dake d'akin yayi yace "A yammacin ranar da d'an uwana zai bar duniya sunyi magana da liman, bayan liman ya min bayani kuma na gamsu d'ari bisa d'ari, dan nasan ba zai fad'a min abinda ba haka ba, bayan liman kuma ya sake kiran *Falmata* ya sanar da ita an tsayar da maganar, hakan ya tabbatar min wannan shine burin d'an uwana na k'arshe, shiyasa na tara mu anan ina neman yardar kowa da had'in kai dan ina so na d'aura auren bayan sallah la'asar a yau d'in nan." Liman ne yace "Yallab'ai wannan ai ba wata matsala bace, nima a yanzu bana da wani buri daya wuce na ga anyi auren nan, da alama burin takawa kenan na k'arshe." Jinjina kai Abba yace ya kalli liman yace "Imran ka amince a d'aura auren nan yau?" Cikin sanda kai k'asa yace "Bana da wata matsala Baffa, na so ace mahaifina yana raye zaiga wannan lokacin." Abba ne yace "To Alhamdulillah, tunda kun amince sai kowa yaje ya fara shirin data kamace shi kafin la'asar." Kamar saukar aradu sai kuwa matar waziri *Asabe* tace "Tab'dijam, lallai ma duniyar nan babu gaskiya, ace mutum lokacin da yana raye ba'a k'ago wannan labarin ba sai yanzu, humm." Kowa kallonta yayi, waziri kuma k'uri yayi da ido yana kallon yanayin Abba, dan yasan in ranshi ya b'ace ba fa da ita zaiyi ba da shi mijinta zaiyi, tabbas Abba yaji maganar har cikin ranshi, dan k'arshen raina masa hankali ne matar tayi, da ace ba mace bace ko kuma a cikin family take da saiya kasheta da mari, amma daya saci kallon 'yar tashi yaga har ta fara hawa sai kawai a ranshi yace "Zan barki da wannan ita ce daidai ke, idan na tabbatar kin shiga hankalinki zai dakatar da tarzomar." Abbas kuma hankalinshi na kan tashi yar rigimar, wani kallo data wa Asabe ne yasa shi rik'e hannunta yana murza yatsunta, gyara zama Sameera tayi da kyau tana kallonta da wani irin yanayi kafin tace "Ke kuma malama waya saka bakinki a cikin maganar family? Ku fa kawai kun zo nan ne fa a matsayin wanda zasu zama shaidu a cikin al'amarin." Sake matsowa tayi gaban kujerar kamar zata fad'o k'asa tace "To wai ma me kike nufi da abinda kika fad'a? Kina nufin mahaifina da liman zasu zauna su k'irk'iri labarin k'arya ne a cikin mutanen da baku fi su kiraku da bayinsu ba? Ke yanzu inba rashin mutumci ba har zaki kalli wannan ki fad'a masa maganar nan, ko kinsan abinda kika fad'a zai iya jaza miki hukuncin kisa ta hanyar rataya?" A kowane sakan ranta ne take ji yana k'ara b'acewa, dan ji take kamar fa matar ta kalli Abbanta ne tace mishi mak'aryaci, ga kuma Abbas dake ci gaba da matsar yatsunta alamar tayi shiru tayi hak'uri, kenan ma yasan da an b'ata mata rai, mik'ewa taje tayi da niyyar tace matar ta fita sai kawai Ammie tace "Kiyi hak'uri takwara, koma ki zauna." Ko kallon Ammie ba tayi ba sai hararan matar take amma dai ba tace komai ba, hannunta Abbas ya kama ya jawo dan ta zauna amma tayi k'yam ta cije, liman ne yace "Hajia Fati kiyi hak'uri ki zauna muyi magana." Hawaye ne taf a idonta ta nuna Asabe tace "Abba na fa take nufin mak'aryaci ne, Abban nawa." K'aramin tsaki Abbas yayi ya mik'e tsaye ya had'e fuska ya kalleta yace "Malama fita anan, taron yara ne a gurin nan da zaki tayar mana da hankali." Juyawa tayi ta kalleshi ido tsaye da nufin yi mishi tas, amma suna had'a ido saiya mata kallon da yasan dole ta shafa mishi lafiya, yau da gobe tasa Abbas karantar matarshi da kuma iya zama da ita, duk zuciyarta da masifarta tana shakkarshi, duk yanda bata barin takwana shi kam tana kwana har ma ta hantse bata rama ba, sai dai inya gaya mata abin ya mata zafi sosai to ta kanyi zazzab'i ko ciwon kai na tsananin bak'in ciki da takaici, wani lokacin kuma kan yara take hucewa duk abinda sukayi saita musu fad'a harta had'a da duka, yanzun ma tana ganin ba zata iya ramawa ba saita juya kan Asabe wacce ita ta jima da tsorata, tunkararta tayi da sauri da niyyar cakumota ta jefar a k'asa... *Wato takwara har yanzu ba'a shiryu ba kenan a gane cewa an girma.* 05/06/2020 à 13:18 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _8_ Washe gari ma tunda asuba suka shirya dan tafiya sadakar uku, a tare aka fito dan tafiya, su Junaid a mota d'aya suke sai Ammar dake tashi motar shi kad'ai kamar maye, wasu motocin har sun fara fita sai kawai Ammar ya fito daga motar shi ya zo ya tsaya gaban k'ofar Junaid dake mazaunin matuk'i, kallonshi yayi ya sauke gilashi yana jiran yaji me zai ce mishi, shiru sukayi sai kallon kallo ake, hakan yasa Amar dake baya zaune yace mishi "Fita ka dawo nan, shi zai tuk'a." Murya k'asa k'asa Junaid ya fito yana fad'in "Iko sai mai shi." Yana komawa baya Ammar ya shiga ya figi motar suka fita daga gidan suma, sun d'auki titi ana tafiya cikin yan uwa, tafiya ake su dai ukun suna hira amma banda shi daya rufe kunnuwa da abin sauraro (écouteur), cikin mintocin da basu kai awa ba sai gasu gidan roumji, kwanar da zaka shiga ta tabbatar da kai cikin garin sauran motocin suka shiga, amma me sai Ammar yayi tazarce zuwa titin tare da k'ara gudu, kallon kallo aka fara sai dai kowa ya kasa magana, Amar ne yayi k'arfin halin cewa "Ammar ina ga fa ka b'ata hanya." Shiru yayi mishi sai ma k'ara birkaka giya da yayi, kallonshi Junaid yayi zaiyi magana Amar ya mishi alama daga nan kar yace komai ya kalleshi kawai, Jibril na ganin haka saiya tab'e baki ya k'ara gyara zama yace "Ai dai duk tsiyarshi ba siyar damu zaiyi ba ko? To fak'at." Amar ne yace "Amma da dad'i musan inda zamuje." Muryar Ammar suka tsinta yana fad'in "Budurwar taka tasan da zuwanka ne?" Da mamaki Junaid ya juyo ya kalli yan uwa suma kallonshi suke, a hankali Ammar ya karkato kai zuwa ga kallon Junaid dan yasan dashi yake, kallonshi yayi shima yace "A'a bata sani ba, ita ai tana nan garin." "Bata sani ba kuma shine zaka je har ka nemi aurenta? Baka tsoron ta d'auka ita ce rayuwarka hakan yasa ta rainaka." Yanda yake maganar yasa Junaid ji kamar mahaifinshi colonel ne ke maganar, dan haka yayi shiru baice komai ba, tsaki Ammar d'in yayi yace "Ku tabbatar idan munje zamu dawo yau d'in nan, dan ba zan iya kwana wani gari ba haka kawai." Tsuru tsuru sukayi da ido suna kallon juna, Jibril ne ya fad'a da k'arfi "Wai kana so kace yanzu can muka nufa?" Yana sharara gudu yace "Hakane." "Amma..." Kasa k'arasawa Jibril yayi sai Amar daya ce "Amma d'an uwa Hajia da su Abba ba zasu ji dad'i ba, kuma ya zamuyi doguwar tafiya irin wannan ba tare da mun sanar dasu ba?" Ba tare daya kalleshi ba yace "To idan har yanzu nono ake baka na aje ka anan mana ka koma ka tsotsa." Shi kanshi Amar saida ya murmusa kafin yace "Kafi kowa sanin dole zamusha fad'a wurin Hajia, haka ma Abba da Ummy." Wata yar iskar dariya Ammar yayi ta gefen baki yace "Kuma kowa anan yasan waye za'a yiwa fad'an ba, ni ne, dan haka ban tsoron duk abinda zasu fad'a, na saba da jin hayaniyarsu a kai na dama." Junaid da shi dai ya ma rasa farin ciki zaiyi zasuje neman auren masoyiyarshi? Ko kuma yaji ba dad'i saboda bala'in da zasu tarar a gida? Dan ya sani dole sai Hajia ta d'auki mataki a kansu musamman taji me suka tafi yi, hakan yasa ya kallesu yace "Amma dan Allah yan uwa mu bar tafiyar nan ta zama sirri, dan in Hajia taji ranmu zai b'ace, ni kuma bana so saboda ni wani abun ya faru daku marar dad'i." Da wani kallo Ammar ya kalleshi yace "Sai me? Ta yanke duk hukuncin da zata yanke, ina da tabbas ba zata yanke mana hukuncin da zai cutar da mu ba saboda muna tare da shalelenta." Ajiyar zuciya Amar ya sauke danya fahimci kamar abun na d'an damun Ammar d'in, wayarshi ya d'auka ya sake danna wa'azin da yake sauraro yana fad'in "Allah ne ya taimaki tsohuwar nan ba'a siyar da bindiga haka kawai, da tuni hankalin kowa ya kwanta a gidan nan idan na wurga mata alburushi a tsakiyar zuciya." Junaid ne ya kalleshi yace "Kakar taka zaka kashe Ammar?" Saida ya harareshi yace "Kakarku dai." Amar ne cikin dariya yace "Ko ba komai fa ta haifi ubanka." Nan ma juyowa yayi ya kalleshi yace "Ubanka dai ta haifa." Tintsirewa sukayi da dariya, kallon Junaid yayi yace "Ina fatan dai kasan inda zamu je? Ba sai munje ba ka samu gillisuwa a tsakiyar garin da ba na ubanninmu ba." Zaro ido Junaid yayi yace "Wallahi da gaskiyarka, ni duk cikin labarin da Iklima ta bani bata fad'a min sunan unguwarsu ba, amma bari na kirata saina tambaya." Jibril ne daga baya yace "Yayi dai zakin soyayya, Allah dai ya kai damo ga harawa." Juyowa Junaid yayi yana cikin neman lambar Iklima yace "Ai ko bai ci ba kai kasan zaiyi b'anna." Danna ok yayi ya d'ora a kunne, ba jimawa sosai ta d'auka suka gaisa kamar yanda suka saba, tambayarta yayi sunan unguwar tace gaskiya bata sani ba, amma ya bari ta kira Mari ta tambayeta, har zai kashe wayar tayi saurin cewa "Dakata." D'orawa tayi da "Da jima wata rana mun tab'a had'uwa da wani mutum a kasuwa babba, sun gaisa dashi sosai har take tambayarshi ya mamanta take, sai naji yace mata jikinta da sauk'i sosai, tabbas koma meye sunan unguwarsu babu nisa tsakaninsu da gidan bus d'in *Sonef*, dan tace min a unguwarsu yake aiki a gidan bus d'in." Godiya ya mata sosai kafin suyi sallama ya fad'awa yan uwan nashi yanda sukayi, shiru motar ta d'auka kowa da waya yana aikin latsawa, inda Jibril ya shiga tunanin inda zaiga yarinyar nan, gashi ko wani ba zai iya tambaya ita ba tunda babu wanda ya ganshi tare da ita, gashi tun jiya da akayi maganar garinsu yaji ya k'agu ya zo garin, yana matuk'ar son ganinta da idonshi, tayi aure? Ko kuma dai ta kasa samun jarumin namijin da zai iya zama da ita? Ko kuma dai... rasa ma abun tunanin yayi sai kawai yayi d'an k'aramin tsaki ya ci gaba da latsa wayarshi, haka suka dinga rarakar hanya ba ji ba gani ba tsayawa komai, dama bus ce idan ta zo *zinder* take tsayawa, amma su basu da dalilin tsayawa dan haka sukayi tazarce, daga zinder zuwa nan sai gasu a awa d'aya wanda yayi daidai da agogonsu k'arfe *11:20*, hakan na nufin sun ci awa hud'u a hanya, Jibril ne ya nuna musu inda gidan motar yake a sanin daya ma wurin, cikin sa'a suka iso sai Junaid dake tambayar gidan malam Muhammad wanda ya rasu shekara bakwai zuwa shida da suka wuce, mutum na farko ne yace bai sani ba, amma mace ta biyu koda ya tambaya tace "Eh na sani, ko ba Baban Maryama ba wacce tayi ciki? Ai yanzu basa waccen gidan mamanta na tare da kakarta ne." Daga cikin mota Ammar yace "Eh ita, ni ne nai mata cikin, na zo karb'an abinda ta haifa ne, ko zaki nuna mana gidan." 🙄 K'uri ta masa da ido tana kallo, wannan wane marar kunya ne? Ganin kallon ya k'i k'arewa yasa shi bud'e murfin mota ya fito tare da d'ora duka gwiwoyin hannayeshi saman motar yace "Ya dai? Ko na tsaya da kyau ne ta yanda zaki ga ko na isa nayi wa mace ciki? Dube ni fa." Ya fad'a yana zagayowa inda suke tsaye tare da Junaid dake ta dariya, _(yan uwa haka fa jarumin yake, yana da sako zance ta yanda dangi ke ganinshi kamar faranci ne ke damunshi na d'an fari ko kuma rashin wayo, ni kuma nace a'a, haka wasu mutanen suke da sako zance ko wane iri ne)_, da sauri matar nan ta matsa tace "Da kun shiga kwanar nan kuka tambaya za'a nuna muku." Da sauri ta wuce ta bar wurin tana mamakin kalaman mutumin, tana gusawa kuma ta fara fad'a ai wanda yayi wa Maryama ciki ne ya zo amsar 'yarshi, a k'aramin gari kuma da baya da maraba da k'auye sai gashi mata wasu har fitowa suke suna lek'e. Suna shiga kwanar suka tambaya aka nuna musu, yaron daya nuna musu suka ce ya shiga ciki ya fad'a anyi bak'i, jim kad'an yaron ya fito tare da wata tsohuwa a bayanshi, masha Allah ta tsufa sai dai k'aramin jiki dake gareta amma doguwa ce sosai, Junaid dake kallonta ji yake kamar Mari yake kallo dan akwai kama a fuskarsu, d'aya bayan d'aya ta kallesu tana k'ara yafa gyalenta a kafad'a tana rufe rigarta munafata, cikin dattako tace "Ina kwananku yan samari." Junaid har k'asa ya duk'a yana fad'in "Ina kwana Hajia." Su Amar kuma daga tsaye suka gaisheta da girmamawa, amsawa tayi kafin ta kalli Ammar da hankalinshi ke kan waya tace "Gashi kuma ban shaida ku ba yara, daga ina haka? Naga kamar ba 'yan garin nan ba." Junaid ne ya d'an kalli Amar hakan yasa Amar cewa "Hakane Hajia, ba garin nan muke ba, yanzu haka daga maradi muke, mun zo wajenku ne da muhimmiyar magana." Da mamaki a fuskarta tace "To! To ba damuwa, Allah yasa alkairi ke tafe da ku." Junaid ne yayi murmushi yace "Insha Allahu alkairi ne." "Shikenan, ina zuwa ko." Ta fad'a tana juyawa ciki jiki a sanyaye, mamakinta me zai kawo zaratan samari haka har su hud'u gidan nan, iya tunaninta ta kasa gane me suka zo nema ko yi a wajensu, da haka ta samu d'iyar Baba zaune kan kujerar k'arfe tana tsiga musu yakuwa da zasuyi miyar taushe da ita wacce tun ranar data yanki jiki ta fad'i har yanzu tafiyarta sai jan k'afa d'aya take, maganarta ma ba duka kake fahimta ba, tsaye tayi gabanta cikin harshen barbarci tace " Bak'i ne a wajen suka zo nan, sunce daga maradi suke, ni dai bana da kowa a can, dama daga Diffa suka ce, sai dai ko wajenki suka zo yan uwan mijinki ne, amma kuma basuyi kama da dangin Muhammad ba, dan gaskiya dukansu kyakyawa da su, wasu ma biyu a ciki kamar buzaye dan gashin kansu ma a murd'e yake, ko shakka babu kuma wannan 'yan biyu ne, amma dai bari na shigo dasu sai muji meke tafe dasu ko?" Saida ta gyad'a kai tare da d'aga harshenta sama ya manne a hak'oran ta na sama kamar yanda maganarta take yanzun tace "Tttoh." D'aki ta shiga ta fito da tabarma babba ta shinfid'a a bakin bishiyar magwaron dake akwai wanda baya 'ya'ya, lek'awa tayi cikin dattako tace "Bismillah ku shigo." Shigowa sukayi suna doka uwar sallama, d'iyar baba ce ta amsa tana kallonsu ita ma d'aya bayan d'aya, izinin zama ta musu suka cire takalmi suka zauna, kaka ce ta wuce ta d'auko k'atuwar mazubin (tarmus) ruwa masu sanyi ta kawo musu, su uku ne suka sha amma Ammar yatsina fuska yayi alamar bai sha, kujera yar tsugunno kaka ta d'auko ta zauna kusa da d'iyar baba ta kallesu a tsanake tace "Yaran nan ina jinku, har yanzu na kasa tsayar da hankali na wuri d'aya saboda tunanin abinda kuke tafe da shi." Kallon kallo suka shiga da tunanin waye zaiyi magana, Amar ne ya fara nuna kanshi yace "Hajia ni sunana Amar, wannan dukansu 'yan uwa na ne, wannan d'an biyu na ne sunanshi Ammar, wannan kuma Jibril, sai wannan Junaid, dukanmu gida d'aya muke, kuma muna zaune ne tare da iyayenmu dukansu, 'yan uwane mu da muke k'aunar junanmu, sannan muna yin komai na mu tare, wannan yasa ma yanzu muka rako d'an uwan mu ya zo gabatar muku da kanshi a matsayinshi na mai son 'yarku." Kallon juna kaka da d'iyar baba sukayi kafin su sake kallesu, d'iyar baba ce cikin salon maganarta tace " 'Yyar mu kuuuma? Wace 'yaa?" Junaid ne ya kalleta da murmushi a fuskarshi yace "Maryama." Yana fad'in Maryama saiji sukayi tace "Ashhh." Suna dubanta suka ga ashe wuk'ar da take yankan yakuwa da ita ce ta yanketa, kaka ce ta karb'e wuk'ar da kwanon tace "Shiyasa tun farko nace ki bari zan gyara da kaina." Cikin yanayin hushi ta kalli Junaid tace "Dama wannan maganar ce ta kawo ku? Maganar Maryama kuka zo yi mana? To kunga ni da idonku anbaton sunanta kad'ai abinda ya jawo, idan kuka k'ara anbaton sunanta nan gaba tafasashin ruwan can zata zubawa kanta." Ta fad'a tana nuna musu tukunyar dake kan wuta gaban d'iyar baba, cikin b'acin rai ta fara yanka yakuwar tana fad'in "Kalleta ka gani, tana zaune akan kujera ne dalilin wannan yarinyar, ita ta mayar min da 'ya haka, ta riga data fad'a ai babu ita babu Mari, nima kuma haka ban san wata Mari a rayuwata ba." Ammar da kai ka rantse kace baisan tsiyar da suke ba ne ya aje wayarshi gabanshi ya kalli kaka yace "Ke dai baki santa ba, amma ita har yanzu tana so da kuma k'aunar 'yarta, shin kinsan meyasa ta yanki kanta da wuk'a daga jin an anbaci sunan 'yarta? Tsoro, fargaba duk sun ziyarceta a lokacin da taji sunan, ba kuma komai ya haddasa mata su ba sai tunanin wane irin labari muka kawo mata a game da 'yarta Maryama, tana jin tsoron kar ace wani mummunan abu ne ya samu 'yarta tilo, kaka, kina zaune da ita ne amma kin kasa fahimtar damuwarta, kin kasa kallon cikin idonta ki karanci rubutun dake cikin zuciyarta, baki zama mai adalci a gareta ba, da kuwa kin zama mai adalci a wurinta, to da kina kwatanta abinda take ji da a zuciyarta da abinda ke kike ji a duk sanda kika kalleta a wannan halin, nasan babu wanda yafi ki sonta a duniyar nan, kamar yanda babu wanda ya kaiki son ganin ta samu lafiya, ki daure ki kalli idonta zaki fahimci ciwo da rad'ad'in data jima tana d'awainiya dasu a zuciyarta." Mik'ewa yayi ya kalli su Junaid yace "Ina daga waje." Da kallo suka bishi dukansu banda d'iyar baba data duk'e kai tana zubar da hawaye, hak'ik'a yaron nan ya birgeta dan ya fad'i abinda shekaru ta kasa fad'a, tabbas ta gane kuskuren da tayi a waccen ranar na yi wa Mari baki, amma ba'a je ko ina ba ta gane kuskurenta, sai dai ina mahaifiyarta ta d'auki zafi sosai dole taja baki tayi shiru, shiyasa ma har idan aka d'auko maganar mari take nuna kamar ita ma ranta a b'ace yake da ita, amma kullum addu'ar ta bata wuce Allah ya dawo mata da ita gida ba, kaka da ita ma sai lokacin ne taji jikinta yayi wani bala'in sanyi har hannayenta sunyi nauyi, tunanin abinda ya fad'a take, a hankali ta juya ta kalli d'iyar baba dake kuka, cikin harshensu tace "Ki kalleni d'iyar baba." Saida ta gama shan majina da share hawaye kafin ta d'ago ta kalleta lokaci d'aya kuma tayi k'asa da kanta, juyawa kaka tayi ta kallesu tace "Dan Allah ina Mari take yanzu?" Junaid ne yace "Tana Maradi." "Kenan can ta tafi bayan munyi watsi da ita? To me take yi acan, wurin kakanta take malam Rabi'u ko kuma Khadi?" Da mamaki Junaid ya kalleta, idan zai iya tunawa Iklima ta anbaci sunan nan, amma kuma a yanda tace ba mazauni ne shi ba, da wannan mamakin yace "Dama kakan nata acan yake?" Cikin sanyin murya tace "Ba can yake da zama ba, amma yana da iyali acan saboda yana yawan zuwa can wajen harkokinshi." D'orawa tayi da "Dan Allah in da gaske kana sonta ka ce mata ta dawo gida, wallahi a yau d'in nan na gane duk kuskuren nawa ne, bai kamata mu mata haka ba, amma ku fad'a min me take yi acan? Wajen wa take zaune?" Junaid ne ya kalli Amar da Jibril kafin ya kalleta yace "Insha Allahu Hajia zan zan dawo miki da ita gida, na jima ina son Mari ta amince da soyayya ta, amma ta k'i yarda dani saboda waccen abun ma daya faru sam babu laifinta , tayi ne dan ceto rayuwar mahaifinta, da kuma ceton mahaifiyarta daga shiga takaba, yanzu haka ma bata san zamu zo nan ba, wata k'awar ta ce ta taimaka mana har muka zo nan, ina so na koma mata da tabbacin kun bar hushi da ita, idan har ta amince ta dawo to zan zo nan na nemi aurenta, dan nan d'in shi ya fi dacewa dana nemi aurenta." Kamar daga sama d'iyar baba ta kalleshi tace "Ya cikin data tafi dashi? Ta haife shi?" Cikin sanyin jiki yace "Ta haife shi Mama, 'yarta tana nan mai wayo sannan mai kama da mahaifiyarta, yarinya ce mai shiga rai." Sake fashewa tayi da kuka harda rufe baki cikin kukan tace "Dan Allah ku ce ta dawo, ina son ganinta ita da abinda ta haifa, ku bata hak'uri dan Allah, nasan bamu mata adalci ba da muka koreta, bamuyi tunanin halin da zata shiga ba idan ta var gida, watak'ila ma taje ta fad'a karuwanci." Shirun da sukayi yasa tayi shiru ta kallesu, ganin babu wanda yace mata komai yasa tace "Zaman kanta ta shiga?" A hankali Amar yace "Mama karki damu, insha Allahu zata dawo gareki, dama mu abinda ya kawo mu kenan." Kaka ce tace "Abinda kukayi ya nuna mana ku 'ya'yan manyan mutane ne masu dattako, da ace ni na haifi uban Mari wallahi da yanzun nan zan baka Mari halak malak, amma bana da wannan ikon tunda tana da dangin mahaifi, duk da suma sun k'i karb'arta a lokacin da mummunar k'addara ta sameta, amma dole hakk'in su ne mu sanar dasu abinda ke faruwa, anyi sa'a malam rabi'u yana garin nan, dan haka yau ba sai gobe ba zanje da kaina na sanar dashi duk abinda ke faruwa, idan zai yiwu ma sai muje tare daku wurinshi." D'an kallon juna sukayi kafin Jibril yace "Ba damuwa Hajia, zamu iya tafiya dan ba anan zamu kwana ba, muna so ne mu sake komawa gida." Da mamaki tace "Amma yaran nan kamar ana korarku, wannan doguwar tafiyar kawai dan wuni d'aya." Nan dai suka nuna mata eh fa komawa zasuyi, dan haka tace bari ta shirya saita fito su tafi, d'aki ta shiga ta sauya kaya da mayafi ta shafo turare na barebari mai dad'i ta fito, nan suka mik'e suka wa Mama sai sun dawo, suna fitowa Ammar na cikin mota zaune da waya a kunne, Amar dai a zuciyar shi cewa yayi "Mai abun tsiya dana kirki, da kana da budurwa da sai nace da ita kake waya." Junaid ne ya bud'e ata gida gaba ta shiga ya rufe, baya suka shiga su uku Ammar yaja motar ba tare da sanin inda zai nufa ba, mutanen da suka fito ganin k'wam ne suka koma tsegumi an tafi da *Magaram*, su kuma suna hanya ta dinga nuna musu wurin da hausarta da basu cika ganewa ba har suka isa dan babu nisa sosai ma tsakaninsu, sunyi sa'a samun malam rabi'u a d'akin shi na soro yana rubutu da allo, nan ma gaisawa sukayi za'a kawo musu ruwa suka ce a'a sun gode, cikin harshen barbarci kaka ta dinga mishi bayani, sun d'an jima suna hira wacce tasa suka fara tsarguwa musamman yanda suka ga malamin yana d'an d'aga murya yana magana cikin fad'a-fad'a, Ammar da ranshi ya gama b'acewa ne yace "Dan Allah ko zaku iya yin yaren da zamu fahimceku? Ko kuma idan maganar bata shafe mu ba ku fad'a mana sai musan inda dare zai mana, amma mu ba k'ananan yara ba, ba kuma jahilai ba mu zauna kuna yi damu." Kallonshi kaka tayi, ita dai duk da ta lura yaron yana da yan matsaloli amma kan daya wayar mata yasa yake birgeta, malam rabi'u kallonshi yayi, (kunsan barebari da fad'a da zuciya) sai kawai ya ga ai tsagwaron marar kunya ne wannan, dan haka ya kalleshi da kyau yace "Magana nake a kan ku, shin ku su waye? Su waye iyayenku a duk garin maradi? Ina kuka san Mari?kuma kuna nufin kun zo neman auren Mari ne ko me? Ina iyayenku suke da ba zaku turo su ba? Ina son sanin amsar wannan tambayoyin yanzu daga bakinku." Duka gira Ammar ya d'aga sama alamar mamaki ido bud'e sosai, gyara zamanshi yayi yanda zaiji dad'in magana, lura da hakan da Amar yayi yasa shi kallonshi yana mishi kallon "Karka siyar mana da halinka dan Allah ko dan Junaid." Cike da jin masifa yace "Kai jira zan bashi amsa ne kawai, to ko tsohuwar gidanmu dake da k'wank'wamai ai ina ji da ita bare wannan malamin." _Yan uwa a yanda labarin gasken ya kasance saboda Ammar yasa aka sha daga sosai kafin rabi'uya ya amince da auren Junaid da Mari, dan yace yaron k'arshen marar kunya ne bashi ba wannan zuri'ar, amma saboda yanayi yasa zan tak'aita masifar dan akwai abubuwa dayawa anan gaba da zasu faru._ Kallonshi Ammar yayi harda alama yake mishi da hannu danya gane yana fad'in "Ni, da wannan da kake gani, uwar mu d'aya ubanmu d'aya, ince dai a garin maradi kasan lieutenant Hassan Gaga? To in ma baka sanshi ba ka tambaya zaka sani, duk wani mai shige da ficen kaya zaisan waye lieutenant Hassan, dan shine babban douanee a garin nan, idan bai yarda ba sai kayanka su shekara dubu a ajiye kuma a wulak'ance." Nuna Junaid yayi yace "Shi kuma wannan d'ane ga colonel Hussein Gaga, shi ma d'in idan baka sanshi ba ka fara kallon tv zaka san waye shi, ko kuma ka zama d'an tada k'ayar baya a cikin al'uma zaka fahimci waye shi." Nuna Jibril yayi yace "In dai har garin maradi kake tabbas zaka san d'an kasuwa Labaran Gaga, wanda yan kasuwa suka bashi matsayin chairman d'in su, dan haka tsoho karka d'auka wata bishiya ce aka girgiza muka fad'o, da kuma nayi niyya wallahi ba zan zo nan da niyyar neman aurenta ba kawai, sai dai na zo da sadakinta a d'aura auren mu tafi da matarmu." Malam rabi'u da al'amarin ya gama zund'umeshi shima kallonshi yayi zaiyi magana sai kuma Ammar yace "Kuma ka tambaye mu wai ina muka had'u da ita? Ai ina ga kamar kunfi kowa sanin inda zamu had'u da ita tunda kun koreta daga gareku, kenan ina kuke son tayi rayuwa?" A hassale malam rabi'u yace "Ka ce idan da kayi niyya da zaka zo da sadakinta? To jini da kyau marar kunya fitsararre, ni kuma bawai ina raye ba, wallahi ko bayan ba raina auren Mari ya haramta gareku, dan ga dukkan alama baku samu tarbiyya a gidanku ba, na ga kuma shafaffe da man daya isa a kaf dangin nan nawa daya isa ya d'aura auren Mari ba da amincewa ta ba." Wata dariya Ammar ya shek'a wacce ko hak'oran shi basu fito ba sai sautin kawai kafin ya tsagaita yace "Ni kuma Ammar in dai har d'an uwana Junaid bai janye k'udirinshi na son auren Mari ba, na rantse da Allah ko saceta ne sai nayi na kuma d'aura musu aure." "A matsayinka nawa? Kai bari dai in mik'e kaga tsawona" Cewar malam rabi'u yana mik'ewa tsaye, Ammar na kallon idonshi yace "A matsayina na yayanshi, zan uya wakiltar iyayenmu akan al'amarin daya shafi dukansu nan, saboda babu wanda ban bawa watanni da haihuwa ba." Jibril da shi dai tun shigowarsu yaji gabanshi sai fad'uwa yake, yana kallon tsohon kuma sai yake ganin wani yanayin mahaifinshi a tare da mutumin, baisan dalili ba amma yaji tsohon ya shiga zuciyarshi daga *kallo d'aya*, tunda suka fara musayar yawun nan yake jin baya jin dad'in abinda Ammar d'in keyi, yanzun ma mik'ewa yayiya kama hannun Ammar ya matse sosai ya kalli tsohon yace " Dan Allah kaka kayi hak'uri, yana da zuciya ne." Malam rabi'u shima sai yanzu ne ya kalli Jibril d'in kallo na tsanake, shi kanshi gabanshi ne ya fad'i, Jibril dake rik'e da hannun Ammar fita yayi da shi waje inda malam ya bi Jibril da kallo, wata zufa ce yaji tana tsatsafo mishi ba gaira babu dalili, take ya fara tuna abubuwan da yayi zamanin k'uruciya wanda har yanzu wannan banzar d'abi'ar bai wani barta ba sai dai in bai samu dama ba, sai dai ya kasa tuna wace uwar ce ta haifa mishi wannan yaron? (Ko kuma ta haifa maka wannan jikan ba, wato shi aiki ko na alkairi ko na sharri dama kana iya mantawa idan kayi, amma wanda kayi wa baya mantawa), Amar da Junaid da kaka ne suka dinga bawa malam hak'uri suna tausarshi, da k'yarsuka shawo kanshi bayan Junaid ya nuna mishi yana so su taimaki rayuwar Mari wacce ke tallar kanta ga kowane namiji yana biyanta, sosai ya jima yana mishi nasiha cikin girmamawa, gamsuwa malam yayi hakan yasa yace ya amince da buk'atarsu, amma indai da gaske yake to dole ya turo iyayenshi dan suyi magana ta manya, alk'awari suka mishi kan zata turo manyansu kafin daga bisani suka mishi sallama suka taso suma. Jibril dake rik'e da hannun Ammar suna fitowa ya fizge hannunshi, bud'e mota yayi ya fito da gorar (bidon) ruwa ya bud'e ya sunkuya yana dararawa a kanshi, saida suka k'are yayi cilli dashi yasa hannu aljihu da niyyar fito da abinda zai goge fuskarshi, lalitarshi ce ta fara fitowa dan haka ya rik'e a d'aya hannun ya sake mayar da hannun aljihu zai fito da shi, kai mai tsautsayi da Allah ya aiko ka kana ganin bak'i ne a garin sai kuwa wani matashin saurayi yayi wup da lalitar ya sura a guje, da sauri da kuma mamaki suka kalli juna shi da Jibril, haba ai saiya mik'awa Jibril mouchoir d'in ya fito da wayarshi a gaban aljihu ya damk'a mishi, da mamaki Jibril ya ke kallonshi yace "Me zakayi Ammar?" "K'ure mishi gudu zanyi." Cewar Ammar dake hangen yaron nata gudu. *Kai jama'a*😂 *Sai A shafi na gaba muji wai da gaske artawa zaiyi ko kuwa zai rabu da wannan daya tari aradu da kai.* _Rashin comment, hummm, saura kad'an ku daina jina._ 05/06/2020 à 20:21 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _9_ Kamar a almara Jibril ya hangi Ammar ya zage k'arfi ya palla a guje ya bi bayan yaron, tuni hankalin jama'a ya koma kansu ana kallo, yanda yake gudun kamar wanda aka ce idan ya fad'i ya rasa gasar shiga soja kenan, shi kanshi gudun da akeyi saiya birgeka, dama kuma haka Allah yake hallitarsa, idan ya maka kyau sai kaga komai kayi saiya maka kyau ko kuma wani yaga kyanka, duk gudun yaron nan saiga Ammar ya cimmasa har yana neman take shi, k'afa yasa ta baya ya harbi nashi k'afafun hakan yayi sanadiyar fad'uwar yaron warwas a k'asa, kafin ya ankara yasan fad'uwa yayi Ammar ya shak'o wuyan rigarshi tare da bank'are hannunshi ta bayan wuyanshi ya murd'e ya amshi lalitar, ba tare daya sakeshi ba kuma ya izo k'eyar shi gaba izuwa inda suka bari, mutane dake kallon k'aramin kafce wasu na tunanin su bayar da hak'uri su raba, sai dai tunanin su yafi basu cewa soja ne duk da cikin wani yadi yake kalar ruwan madara shara-shara, dan haka meya kaisu shi ma yaron tsautsayi ne da kuma k'arar kwana, yaron da yaga Ammar na dawowa dashi fashewa yayi da kuka yana so ya durk'ushe ya bashi hak'uri amma ya k'i barinshi ma ya kai k'asan, cikin kuka dake nuna tashin hankali yake fad'in "Dan Allah baba na kayi hak'uri, wallahi yunwa ce tasa nayi maka k'wace, ka rufa min asiri kayi min rai." Ko saurarenshi baiyi ba har suka zo inda Jibril ke tsaye mamaki ya gama kashe shi, suna zuwa Amma ya jingina ga koma ya saki yaron ya kalli Jibril yace "Ban hankici (handkiciep) na." Mik'a masa yayi yana kallon yaron da tsoro ya gama bayyana a tare da shi kamar ya ga mala'ikan d'aukan rai, yana cikin goge zufar dake tararowa kanshi zuwa fuska da wuyanshi ya kalli yaron yace "Durk'usa." Kamar marar k'ashi a jiki haka ya lauye ya durk'ushe yana sake fad'in "Dan Allah kayi hak'uri baba na, wallahi ni ba b'arawo bane tsautsayi ne da yunwa, dan Allah magajina ka bashi hak'uri kar ya kaini prison (magark'ama)." Ya k'arashe maganar da duban Jibril, idon nan sun kad'a sunyi jawur ya kalli yaron da kyau yace "Kai, kasan ko wanene ni?" Da sauri ya girgiza kai yace "A'a." "To meyasa duk garin nan ka rasa wa zaka figi kayanshi sai ni?" K'uri ya masa da ido yana kallo jikinshi banda rawa babu abinda yake, hannu ya d'aga kamar zai mareshi yace "Da kai nake kana jina ka min shiru." Cikin kukan firgici yace "Wallahi yunwa ce tasa, kwana biyu ban ci komai ba, kuma nayi bara ban samu abinda zan ci ba shiyasa, dan Allah kayi hak'uri ka gafarce ni." Fuska a had'e yace "Ina iyayenka suke?" Ba tare daya tsagaita kukan ba yace "Ba yan garin nan bane, suna zinder ne, almajiranci suka kawo ni." A lokacin ne su Junaid suka fito sun gama tattaunawa, Amar ne yayi saurin ciro wayarshi ya duba mai kira, saida gabanshi ya fad'i ganin Hajia ce, Junaid daya fahimta yace "Karka d'auka tunda yanzu zamu koma, gwara musha giyar ta dubu sai ayi kankat." Wayar ya kashe tare da jefata aljihu a lokacin ji sukayi kawai Ammar yace "Shiga mota zan mayar da kai gidanku." Pik'i-pik'i yayi dan shi dai bai bai yarda gidansu zai kaishi ba, amma tsoro yasa ya mik'e yana d'an rakub'ewa da d'ar-d'ar har ya shiga inda su Junaid suke, saida suka d'auki hanya Amar ya tambayi Jibril meya faru? Jibril da yake tunanin wai Ammar wane irin mutum ne? Anya wannan ba Allah ne ya dubesu ba ya k'i bashi aikin sojan da yake so, girgiza kai yayi yace "Kai dai abar kaza cikin gashinta kawai." Junaid ne yayi dariya a harshen fransanci yace "Dan Allah ka bamu musha mu ma, meya faru?" Nan Jibril ya canza harshe shima ya fad'a musu, ba jimawa kuma sun iso gidansu kaka, ko cikin gidan basu shiga ba sukayi alwala suka shiga masallacin dake kusa da su sukayi sallah, nan kaka tace su shigo su ci abinci, basu mata musu ba suka shiga ciki suka zauna kan tabarma, shinkafa ce da miyar taushe (tauhe 😂) aka kawo musu, sai ruwan sanyi a gafe suna korawa, duk da Ammar sai wani had'e fuska yake amma har ranshi miyar ta birge shi, tare da almajirin nan suka ci har suka ida sukayi hamdala, nan suka musu sallama suka tafi tare da cewa sai sun dawo, daga nan suka sake d'aukar hanyar komawa gida. *Gidan roumji* Suna sauka suka fahimci babu motar yaransu samari wanda suke jinsu kamar wasu garkuwarsu ne idan suna tare da su, mamaki suke ko lafiya, amma sai Labaran yace watak'ila ko motarsu ta samu matsala dan k'arfen nasara babu tabbas, a haka aka bar maganar aka shiga abinda ya tara kowa, har akayi addu'a aka gama aka kwashe awa d'aya babu su babu labari, nan aka fara kiran wayoyinsu amma a lokacin suna hanya akwai matsalar hanyar sadarwar yasa kiran ma baya shiga, wannan abu ya basu mamaki hankali kuma ya fara tashi, lieutenant da ranshi ya b'ace ne yace kar wanda ya sake kiransu, ai babu yaro a cikinsu, kuma da idonshi ya ga motarsu biye dasu har cikin garin nan, dan haka ba musakai ne ba zasu iya k'arasowa k'asa ai, idan kuma hakan ya gagara ai zasu iya kiransu su fad'a musu, dan haka yace su k'yalesu kawai su zuba musu ido, amma basu bari Hajia taji me ake ciki ba, duk da kowa ya bar maganar a zahirance amma haihuwa ta shiga tsakaninsu da b'acin ransu, kowa da abinda yake tunani a ranshi a game da nashi yaron da sauran yaran, a hakane fa har lokacin sallah azahar yayi, lokacin ne Hajia tace ayi haramar tafiya gida dan ita ta gaji da zaman k'auyen nan, a lokacin taji abinda ke wakana, kafin tace komai ne ta kira lambar shalele amma bai d'aga ba, tana sake aika wani kiran kuma sai aka ce wayar kashe, lokacin ne ta rufe ido ta dinga surfa masifa a cikin gidan har akayi sallah hankali ba kwance ba, kuma abinda yafi damun lieutenant da Sa'ada shine cewa da take wannan d'an banzan Ammar d'in ne ya d'auke mata shalele, ita bata ma san ina ya kaishi ba, inda Zeinabu ta tabbatar lallai Hajia bata k'aunar nasu yayan saina Sa'ada suma kuma d'a d'aya take so, Soueiba kuma ta k'ara yarda bata son duk wani jini daya fito daga jikin sarakuwarta Husseina, Alhaji kuma yana ji ya zuba mata ido dan in yace yayi magana zata mishi rashin mutumci ne cikin mutane, dan haka kawai yake kallonta har tayi ta gama, a haka dai tasa suka sake dawowa gida dan ganin meke faruwa. Tashin hankali, labarin da suka samu a gida ma shine ai tare kuka fita dasu, cikin masifa Hajia tace "Kuma basu dawo ba?" "Basu dawo ba Hajia." Cewar Nana mai aiki, cire gyalenta tayi da jakarta ta aje ta zauna kujerar falo tana rau da kanta, duk wani motsin Sa'ada saita kalleta, hakan yasa ta kasa motsawa daga inda take saboda gudun karta zargeta, sallah la'asar kad'ai tasa kowa ya gusa daga falon dan gabatar da sallah, haka gidan ya ci gaba da zama shiru Hajia kuma na zaune a falo ta kasa ta tsare sai taga shigowarsu, inda Alhaji ke zaune a bayan gidan iskan 'ya'yan itatuwa na kad'a mishi. *Saida* wannan yaron ya nuna mishi har k'ofar gidansu saidai kamar suna k'uryar gari ne, yaron na fitowa Ammar ya ciro lalitarshi ya fito da kud'i, jaka goma goma guda uku ya bashi yace "Wannan kayi sana'a dashi, idan kuma na sake ganinka a irin wannan banzar rayuwar wallahi saina lahira yafi ka jin dad'i, kasan dai da aljanuna zasu iya nuna min duk inda kake ko?" Da sauri yaron ya dinga girgiza kai alamar eh kamar k'adangare, jinjina kai shima yayi alamar ah to ka ma shiga hankalinka kafin ya sake had'e fuska yace "Idan kuma ka shiga gidanku ka ce da iyayenka shugaban *sojojin niger* (general) ne ya dawo da kai yace ka zauna gida, idan har suka sake mayar da kai..." Saida ya kalli gabanshi ya d'an cije leb'e ya kalli yaron yace "Ka fad'awa mahaifinka da kaina zan sauke mishi kafad'a ta hannun hagu." Da sauri yaron yace "Babana ya rasu, nan daga mamata ne sai k'annan Baba na." Zaro mishi ido yayi cikin d'aga murya yace "To su k'annan baban na ka basu da kafad'a ne?" "Suna da." Ya fad'a a muryar kuka, wani jinjina kai yayi alamar jin dad'i yace "To ka fad'a musu haka." Yana fad'a ya d'aga gilashin motar ya fizgeta da k'arfi ya tayar da k'ura suka koma baya dan su hau titi, yaron da baki sake saida ya ga b'acewar motar ya juya gida, tunaninshi wannan ba wai aljanu ne dashi ba, shi da kanshi ne aljanin, amma inba haka ba taya kawai zai d'auko ni ya dawo dani? Yanzu karatun nawa fa da nake duk da yunwa bata vari na ma fahimta? Ya malaminmu zaiyi? Ya k'annan babana da kakata zasuyi idan suka ga na dawo? Zasu d'auka tserewata nayi ai tunda dama banso nayi nisa da uwata ba, da wannan tunani barkatai ya shiga cikin gidan, duk abinda aka fad'a mishi ya fad'a sai dai bai fad'i gaskiyar dalilin rabuwarsu ba, gidan tunda suka ji yace shugaban sojoji ma suka sha jinin jikinsu, kakar yaron wacce ta haifi babansu ce tace ma autan ta ai a kwaso duk yaran dake sauran garuruwa su zo nan suyi karatun, dama can yawan gidan ne yasa suka rage ta hanyar turasu almajiranci. Su Amar banda dariya babu abinda suke, amma Ammar kamar baisan sunayi ba sai tuk'i da yake, a *Ague* sukayi sallah magriba suka sake wucewa, wannan karan ba jimawa suka shigo cikin gari sai dai anata sallah isha'i saboda tsakanin lokacin dama ba wata tazara ake samu ba, sannan gashi Ammar ba wani gudu sosai yake ba da zai kawosu gida cikin k'ank'anin lokaci, suna kaiwa *immeuble Gago* ya taka birki ya juya yana kallonsu, Junaid dake gaba ne ya washe baki saboda hango mai gasa kaza da yayi ya kalli su Amar yace "Kai 'yan uwa, babban yaya fa kaji zai siya mana mu ci, kai Allah dai ya k'ara girma yayanmu." Wani jan kallo Ammar ya mishi yace "To jikan kura, kazar uwar wa zan siya muku? Sai kace na d'auko karuwa a mota zan tsaya siyen nama a hanya?" Jibril ne ya kece da dariya yace "Wato ita karuwa idan aka d'auko ta sai an siye nama?" Ko kallonshi baiyi ba sai gani da sukayi ya bud'e ya fita ya zagaya mazaunin Junaid, da sauri Junaid ya fito ya dawo mazauninshi ya tayar da motar suka fara tafiya, cikin masifa Ammar ke fad'in "Shegu 'yan banza, ai dama zura muku ido nayi naga mai hankalin da zai iya karb'ar tuk'in nan a hanuna, ashe duk k'ananan marasa mutumci ne ku." K'wafa yayi sai Amar da yace "Yi hak'uri yaya, ni wallahi in so na karb'a amma a raina kuma nace watak'ila dan kana babba ne shiyasa ka hutashe da yan uwanka ababen soyuwarka." Wata ashar ce ya malmalo irin ta yan zamani yace "Na soya mata..." Gyara zama yayi ya jingina tare da lumshe ido yace "Ku tanadi abinda zaku fad'awa tsofaffin can, dan ni nan banga abinda zai sani magana ba." Kallon kallo suka fara, ai kuwa sai suka fara shiga k'irk'iro labarin da zasu fad'a a gida wanda zai dace da hankali, suna tsaka da haka Ammar da idonshi ke rufe yace "Ya kamata kusan cewa da Allah yana so ku zama sakarkaru to fa daya halliceku babu baki, akan me zaku musu k'arya? Duk cikinku akwai wanda zai tsireku ya rataye? Ko kuma akwai mai wutar da zai saka ku a ciki? Kunga, ban yarda na biku ba saida na tabbatar aikin alkairi muka je yi, amma kuna so ku mayar da kanku lusarai kamar ba maza ba, a hakane yanzu kuke so kuyi aure, to ya zakuyi da matan?" Cikin turo baki irin na shagwab'a Junaid yace "Yanda kowa yake yi da su mana." Tsaki Ammar yayi ya bud'e ido ya kalleshi yace "Shin ko kasan a cikin maza akwai mata-maza? Sannan akwai muna-maza, kamar yanda ke akwai mun rako maza duniya, to zaku kasance d'aya daga cikin ukun nan ne in kuka ci gaba da haka." Amar ne yace "Ammar zafa mu baka mamaki wallahi, ai namiji zai amsa sunanshi ne a lokacin da yake iya ciyar da matarshi, yake mata sutura iya iyawarshi, yake kula da lafiyarta da addininta, sannan yake gamsar da ita a shinfid'a." Murmushi yayi wanda Junaid dake gaba ne kad'ai ya gani kafin yace "To ko ita gamsarwar da kake magana a kai tana buk'atar zarra, sai ka zama namijin gaske kafin ka gamsar da yan matan yanzu, idan kuma ba haka ba wallahi kaine zaka wahala har ka zubar da hawaye, dan irin kayan da suke anfani dasu wajen gyara jikinsu sunfi k'arfin tunaninka." Jibril ne ya d'an lek'o kai ya dafa kafad'ar Ammar yace "Babban yaya ince dai in zamuyi aure kai zaka zama malamin mu?" Bige hannunshi yayi ya juyo a harzuk'e yace "Saboda d'an iska ne ni?" Kwashewa sukayi da dariya, suna tsaka da dariya yace musu "Billahil-azeem duk wanda ya fad'a musu k'arya saina tona asiri, dan ni ba zan yarda ayi k'arya dani ba." Da haka dai suka iso gida suka danna ham (😂) mai gadi ya bud'e musu suka shiga, a wajen ajiye motoci suka paka ta su kafin suka fito cike da gajiya, cikin wani takon izza da k'asaita Ammar ya nufi b'angaren su, Junaid ne yace "Ammar ka zo mu fara shiga ciki dan Allah, ni nafi son ayita ta k'are." Tsaye yayi ya juyo ya kalleshi yace "Kai ne uban tafiyar ai, ka fara shiga ciki ka fara d'aukar naka rabon, ni daga baya na shigo bayan nayi wanka." Jibril ne yace "Amma dai da mun fara shiga a mana bala'in, in ya so daga baya ma huta gajiyar." Rai had'e yace "Na ce wanka zanyi ko." Amar daya d'an lek'a kusa da falon Hajia ne yace "Ka zo muje dan Allah, wallahi nasan mu suke jira dan ayi magana." Juyawa yayi ya fara tafiya yana fad'in "To duk wanda ba zai iya hak'ura na fito daga wanka ba kuce su sameni a ban d'akin sai muyi maganar." "Kana wankan?" Cewar Jibril yana zaro ido, ba tare daya juyo ba yace "To meye a ciki, su d'in iyayena, ku kuma yan uwana ne maza, hallitar iri d'aya ce, ko kun kalla babu abinda zaku ji a ranku, wannan tsohuwar ce ma kawai bana so ta ganni babu kaya, kallon data min ina yaro ma ya isa haka, taje ta kalli mijinta." *Ma Sajida sai kin taimaka min da lema (para-pluie) wacce zan dinga kare wannan katob'arar fa, dan wani abun idan ya murguzo kasa duk'ewa nake.* Lieutenant da yake son fita amma Hajia tace babu inda zashi sai yaran sun dawo taji daga inda suke, yana jin k'arar motar ya fito ya duba, ai kuwa a lokacin da Amma ke tafiya zai bud'e k'ofar b'angaren su suka ji yace "To ku wuce muke ciki." Take suka fara rarraba ido suna kallon kallo, kamar wanda k'wai ya fashe ma a ciki haka suka fara tafiya, murmushi Amar yayi yace "Abba barka da dare." Dak'uwa 🖐️ ya watso mishi tare da nuna musu hanya su wuce gaba, Ammar dake kallon abinda ke faruwa baida niyyar tahowa, lieutenant ne yace "To ubana, sai nayi magana ko?" Wani farrrr yayi da ido kamar mace na son karb'ar kud'i hannun mai gida kafin ya taho ciki takun k'arfi, saida ya kawo daf dashi zai wuce lieutenant ya d'aga hannu da nufin bugunshi a k'eya, da sauri ya duk'e tare da ja baya ya d'ago yana kallonshi yace "Abba wai sau nawa zan fad'a maka ka daina sarar dukana a kai? Kayi karatu fa, ko dai ka manta abinda ka karanta ne a cikin aji game da abubuwan dake cikin kai?" A hassale lieutenant yayi kanshi ya zura hannu zai shak'o wuyanshi ya sake zillewa, tsaye yayi yace "To wai yanzu dukana ne kake so kayi ko me? Kasan dai na wuce wannan matakin ko?" Saida ya nuna shi da yatsa yace "Dan Allah ka zo nan ka gani idan ban dake ba, Ammar ni zaka raina ka mayar wani mahaukaci." Saida yayi nesa dashi ya ya wuce ya nufi falon Hajia yana fad'in "So ne kawai yake a kafa min mugayen hak'ora, ya bini a guje ya fad'i shikenan ace na kashe ubana, haba, tsofi sai jaraba bakinsu ko ciwo baya yi." Yana dosowa falon ya canza salon tafiya da yanayin fuska irin ba magana kuma ba wasa bare dariya, yana shiga ya samu su Junaid sunyi cirko cirko zaune a k'asa kowa kanshi k'asa, gefenshi ya kalla inda Ummy, Soueiba da Zeinabu suke zaune, sai gefe guda su Amna ne da Umaima ke ta latsar wayar amma banda Hamna dake shan kankana da cokali mai yatsu, "Wato dan raini a gaban yaran nan za'a musu fad'a? Kai ba zai yiwu ba gaskiya." Kallonsu yake yana so su kalleshi ko zasu fahimci kallon amma rashin sa'a babu wacce ta kalle shi har kankanar ma, a hankali ya cire takalmi ya k'arasa kusansu Junaid, amma saboda iko sai yayi zaune akan kujera yana kallonsu su dake k'asa kamar sun zo d'aukar karatu, Ummy ya kalla wacce idonta ke kanshi kamar ta zundumo mishi zagi, kallon Husseina yayi dake zaune kujera d'aya da Labaran da kuma Alhaji, hannu ya d'aga musu ba alamar fara'a yace "Barkanku da dare." Husseina dake ta doka uban murmushi ce ta amsa mishi da "Barka Ammar." Hajia ya kalla wacce bata da niyyar magana har yanzu, a ranshi yake fad'in "Wannan indai ba shanye Alhaji kikayi ba me zaisa gashi zaune amma ke ce mai zartar da hukunci, Allah ya sawak'e miki." Ganin har yanzu shiru yasa ya kalli mutanen d'akin "Idan an gama karatun saimu rufe da salatin annabi ko?" Su Amar dake kusa dashi duk rik'e dariyarsu sukayi, hakan ya hassala Hajia ta mik'e tsaye da fad'in "Kaiiiii." Yana jin haka saiya jingina a kujera ya d'ora hannunshi a matangalin kujera yana shafar k'ulun hallitar dake mak'ogwaronshi wanda bak'in gashi mai silb'i ya rufe shi, kallon yan k'asa tayi dan sunfi dama dama tace "Daga ina kuke?" Shiru ne ya d'an ratsa wurin yayin da Junaid ke ganin ba zai yarda a d'ora musu laifi ba, dan haka ya d'ago ya kalleta yace "Daga Goure." Yatsina fuska tayi ta kallesu da kyau tace "Me kuka je yi a Goure? Wa ma ya aike ku?" Junaid dake jin wani sanyi na ratsa zuciyarsa babu fargaba yace "Munje sulhunta tsakanin Maryama ne da iyayenta, sannan na gabatar da kaina a matsayin mai son aurenta, kuma sun amince." "Wacece hakanan kuma?" Hajia ta tambaya cike da rainin wayo, shiru ya d'anyi dan haka ta kalli Zeinabu dake kallon Junaid da mamaki tace "Ke kinsan wacece hakanan?" Cike da ladabi tace "Umma ita ce yarinyar da yace yana..." Bata bari ta k'arasa ba tace "Ku ce min karuwa, wai karuwa kake nufi? Neman aurenta kaje kenan ko me?" Shiru dukansu sukayi, cikin taushin murya tace "Shalele, har da kai da nake ganin kamar kana da hankali? Ya zaka biye musu wajen yin wannan d'anyan aikin? Halan wani ne ya tilastaka?" Ta fad'i hakane tana kallon Ammar da shima yana jin haka ya kalleta, dan yasan shi take nufi, d'auke idonshi yayi dan haka Amar yace "Babu wanda ya tilasta ni, kawai naga yan uwana zasu tafi ne ni kuma na tafi tare da su." D'aga kai tayi sama cikin gadara tace "Hakan na nufin kenan kun girma? Kun isa ku yanke hukuncin daya shafi rayuwarku ba tare da sanin kowa ba, hakan na nufin zaku iya ji da al'amari komai girmanshi idan ya taso muku ba tare da shawarar ko da iyayenku ba, to da kyau, amma ku saurare ni kuji." Fuskantarsu tayi da kyau tace "A gidan nan ba ayi ba ba kuma za ayi wanda zai taka min doka ba ya kwana lafiya, matuk'ar ina raye banga wanda ya isa a gidan ya dinga juya rayuwarshi yanda yake so ba, dan haka tunda kun nuna min zaku ja dani, ni kuma zan dakatar da al'amarin yanzun nan." Juyawa tayi ta koma inda take ta zauna ta d'ora gwiwoyin hannunta a saman cinyarta kafin tace "Hutun makaranta da za'a bayar na kwana goma nan da sati uku, ku shirya mishi da kyau, dan aurenku za ayi." Da sauri suka d'ago suka kalleta inda Ammar ya dakatar da shafar gemun da take yana mata kallon mai bisa ruwa, jinjina kai tayi da yake nuna tabbas babu fashi tare da d'orawa da " *Shalele* zaka auri 'yar uwarka *Umaima*, *Junaid* zaka auri 'yar uwarka *Hamna*, kai uban sarkin marasa kunya zan had'a ka da wacce baka isa kace ta maka laifi ba bare harka zalinceta ( *Ammar*), za'a d'aura aurenka da *Amna*." Juyawa tayi ta kalli Jamila sannan ta kalli Jibril, ita dai badan tana so ba zata had'a tsatsonta dana Husseina, amma idan ba tayi ba yanzu tsohon na zai kawo mata cikas a lamarinta, dan haka tace "Kai kuma *Jibril* zaka auri Jamila, wannan shine hukunci na, da wani mai ja." Ta fad'a tana kallon iyayen duka, amma cikinsu sai kowa ya girgiza kai harda arhar murmushi da suke mata ana fad'in ai duk gida ne dan haka abun farin ciki ne, da murmushin k'asaita tace "Ku tashi ku bani wuri." Mik'ewa sukayi kamar babu lakka a jikinsu, amma Ammar ko niyyar tashi ma baiyi ba, sun fara tafiya tace "Shalele." Juyowa yayi tace "Idan kayi wanka ka ci abinci ka same ni d'aki na." "To." Kawai ya fad'a suka bar falon, kallon Ammar tayi tace "Ko saina tasheka ne kai kuma?" Saida ya d'an harareta na wucen gadi kafin ya mik'e ita kuma tsaf ta gane hararenta yayi, dan haka ma tace "To ko da magana ne?" Cikin takonshi na isa yace "Ke ma kisan ai idan da maganar zan fad'a, dan bana tashi da kwananniyar magana a baki na." Hamna ce ta saki cokalin hannunta saboda wani abu da taji, juyowar da Hajia tayi ne tasa ta saurin d'aukar cokalin, mik'ewa tayi ta aje farantin kankanar ta fita farfajiyar gida, Amna kuma Inna lillahi kawai take maimaitawa, wai da gaske ita ce aka had'a da Ammar? Tab', lallai sunanta margayiya daga yau, to ita ta ina zata iya da auren Ammar? Mutumin da idan ya fad'a maka wata maganar sai kayi sati kana kuka, shine zatayi zaman aure dashi? Umaima kuma har cikin ranta zab'in ya mata, dan dama Amar na masifar birgeta, haka ma Jamila sam bata ji a ranta wai an tauye ta ba, sai dai ta d'auka zata fara shan bikin yayunta ne dan ita ce k'arama a duk cikinsu, to amma haka Allah ya so sai fatan alkairi kawai. Suna shiga b'angaren su kowa wanka ya shiga cikin matuk'ar sanyin jiki, amma banda Ammar da shi sam baiji wani abun bak'in ciki ba, hasalima yace Amna dai ce ta shigo d'akin shi a matsayin mata, Allah yasa ta mata shirin da zata uya zama da shi, duk ranar daya samu wacce zuciyarshi ke *so* to ko a yau Amna ta zo gidan saiya fad'a kuma saiya aureta babu mai hanawa. *WAIWAYE* _(ADON TAFIYA)_ *Suley Hassan Gaga* 05/06/2020 à 20:32 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 _Allah ba dan mu ba ka yafe mana zunubanmu, Allah ba dan halayenmu ba ka gafarta mana kurakurenmu, Allah dan rahamarka ka jik'anmu ka mana gafara, *Astagfirullah wa atubu ilaikh*._ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya madaurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _10_ *Suley Hassan Gaga* Haifaffen garin *Marad'i* dake jamhuriyar Niger, a wata unguwa da ake kira *d'an gulbi*, mahaifinshi Alhaji Hassan yana da mata biyu, ta farko ita ce *Rumanatu* wacce suke kira da Ramma, tana da 'ya'ya uku, babban shine *Innusa* (Yunus), sai k'anwar shi *Barira*, sai kuma k'aramar *Rahmatu*, sai matarshi ta biyu *Saratu* wacce ita ce mahaifiyar Suley da 'yan uwanshi mata 'yan biyu masu sunan *Hassana* da *Husseina*, iyalin Hassan Allah ya musu baiwar haihuwar yan biyu, hakan yasa a ahalin nasu suke da yan biyu masu yawa maza da mata, Ramma na da 'ya'ya uku namiji d'aya da mata biyu, sai dai kasancewarta shu'umar mace yasa ita ke juya gidan da mutanen cikin shi. Hassan yana da tarin arzik'i kama daga shanu zuwa tumaki da gonaki, a zamaninshi yana d'aya daga cikin masu kud'in da ake lissafawa a garin maradi da kewayenshi, amma dayake ya samu hatsabibiyar mata data riga ta gama mallakeshi da sihiri saiya zamana dashi da talaka duk d'aya, domin kuwa gidanshi ma ba'a cin abinci mai kyau bare suruta, tunda Saratu ta shigo gidan take fuskantar matsi daga gareta inda ta mayar da ita kamar baiwa a gidan mijinta, duk wahalar gidan ita ce har lokacin da rabon 'ya'yansu ya koka suma suka durmiya cikin wahalar, duk da kasancewar Suleymane babba kuma namiji amma haka ya zama kamar d'an daudu dan duk wani aikin gida na mata babu wanda bai iya ba, haka suke wannan rayuwar kamar bayin da aka siyo da kud'i dan babu wanda zasu fad'a ma ya taimakesu, duk da lokuta da dama Husseina na basu matsala dan ita ce marar hak'uri, amma haka zatayi saboda uwar na tausarta da cewa tayi hak'uri wata rana sai labari. Saratu dama marainiya ce ba uwa ba uba, k'anin mahaifinta ya bayar da aurenta ne saboda dukiyar Alhaji Hassan, hakan ne yasa babu wanda suke kaiwa kukansu ma bare su saka ran za'a share musu, a cikin wannan bautar da k'ask'anci tafiya tayi nisa yara duk suka mallaki hankalin kansu, 'yan matan sun zama cikakkun 'yan mata da suka isa aure, haka shima Suley ya girma sosai, sai dai matan kamar mujiya suke a cikin tsuntsaye saboda bak'in jini, domin kuwa babu mai kallonsu da sunan so ko k'auna, abun duba kuma shine gasu kyakyawa saboda sunyi kama da mahaifiyarsu wacce ita d'in asalin *babarbara* ce ta *Diffa*, amma haka suke ba mashinshina sai wahalar gidan ubansu kamar zata kashesu, a cikin haka Hajia Ramma ta aurar da yaranta mata, aurensu kamar samun wani kasone daga 'yancin Saratu da 'ya'yanta, dan dama da suna gidan har wankin kayansu su keyi, duk wani abu da zaisa su motsa jiki to saidai susa su musu, dan haka wahalarsu ta ragu da sukayi aure. Shekaru sun kuma ja dayawa amma su Hassana har yanzu babu ma-nemin aure, hakan ya fara damun Saratu fiye da zato ta yanda har ta kan zubar da hawaye idan ta gansu masha Allah sunata yawo a tsakar gida, sai dai bata san meye matsalar ba kuma, wannan ne yasa wata rana wata mak'wabciyarsu mai sunan *Delu* suna daka a tsakar gidan saboda Ramma bata nan take fad'a mata ta tashi tsaye akan yaranta, dan ko shakka babu akwai sihiri a jikinsu daya hana su aure, bud'ar bakin Saratu cewa tayi "To yanzu Delu meye abunyi? Wallahi lamarin yaran yana damuna sosai, kawai dan banda abokin shawara ne." Da sauri Delu tace "Haba ke kuwa Saratu, ai mun zama d'aya, damuwarki damuwata ce, akwai abunyi kam in zaki yarda." Cike da damuwa tace "Zan yarda mana Delu, idan ban samu mafita ba zan saka yaran a gabane na dinga gatsarsu ina ci? Kawai ki fad'a min kedai." "Yawwa Sarai, kina ji ko." Ta fad'a tana yin k'asa da muryarta ta ci gaba da cewa "Akwai wani malami dana sani can bayan gidan sarki idan kin gangara tudun nan, wallahi yana bada taimako sosai dan aikinshi kamar yankar wuk'a ne, to ina tabbatar miki da zaki same shi da matsalarki wallahi zata zama tarihi." Jim ta d'anyi kafin tace "Da gaske Delu? To amma ai matsalar ita ce ni ba komai gareni ba kinsani kema, ko abinci mai kyau ba samunshi muke a gidan nan ba, to taya zan samu kud'in da zan bayar a matsayin sadakar aikin da za'a mana?" Dafa kafad'ar ta tayi tace "Haba Saratu, ni da ke fa yanzu mun zama d'aya, idan da ba zan taimaka miki ba aida ba zan fara fad'a miki maganar malamin nan ba ma, dan haka ki kwantar da hankalinki, insha Allahu zan rakaku idan kun tashi tafiya, kuma ni nan zan sayar da d'aya daga cikin awakina dan ganin yaran nan sun samu mijin aure." Cikin farin ciki Saratu tace "Da gaske Delu? Kai amma naji dad'i da wannan taimakon da kika mana, Allah ya biyaki da gidan aljanna." "Ameen." Ta fad'a tana d'aga tab'aryarta sama suka ci gaba da daka, suna haka Ramma ta shigo gidan, saida ta k'are musu kallo kafin tace "Yanzu dan na fita daga gidan shine har da min gayyar tsiya a gidan nan, to yayi kyau bari Alhaji ya dawo gidan sai ki fad'a mi shi abinda matar nan take yi, dan na tabbatar gulma kukeyi tunda ai bata zuwa gidan idan ina nan." Durk'usawa Sarai tayi har k'asa tana fad'in "Dan Allah Hajia kiyi hak'uri na tuba, wallahi ba zamu sake ba daga yau kiyi hak'uri ki min rai." Delu ce tace "Kinga Saratu tashi, ni zan tafi kar na ja miki matsala ba da niyyar haka na shigo ba, amma dai ya kamata ki rage tsoron nan tunda miji ba shi ya hallice ki ba." Da kallo kawai Sarai ta bita a zuciyarta kuma tana fad'in "Dan baki san bala'in shi bane Delu akan matar nan tashi, ke dai Allah ya mana tsari da irinsu Hajia kawai." Dan kuwa tasan inhar ta fad'a mishi to fa ya mata k'aramin hukunci shine ya mata dukan tsiya bayan idon 'ya'yansu, shine ya mata gata kenan, masifa Ramma ta ci gaba da yi ai kawai munafurci ne ya kawo Delu tunda bata cika zuwa gidan ba musamman ma idan tana gidan, Husseina da Husseina suna d'akin Ramma d'aya na gyaran d'akin d'aya na shara, suma tana shiga ta balbalesu akan basu gama gyaran ba tun lokacin data bar gidan, nan fa ta had'e su ta zage son ranta, da magrib Sarai da 'yan biyu suna zaune a d'akin su sai fitar k'wai (aci balbal) dake bayar da haske, Sarari ce ta lek'o a hankali tsakar gidan taga babu kowa, dawowa tayi ta kalli Hassana tace "Husseina, kinga yi sauri kafin Babanku ya shigo ki tambayo min Delu ki ce nace yaushe ne tafiyar nan, idan ta fad'a miki sai ki ce nace ni ba zanje ba amma ku zaku tafi tare da ita." "To." Kawai Husseina ta fad'a ta tashi ta fita tana waiwayen d'akin Ramma, tana fita Alhaji Hassan kuma ya danno kai cikin gidan, kamar kullum kai tsaye d'akin Ramma ya nufa, tana jin motsinshi ta fashe da kukan makurci, nan fa hankalinshi ya gama watsewa Ramma na kuka, bai samu nutsuwa ba har saida yaga tayi shiru ta fara zayyana masa abinda ya faru kamar haka "Gaskiya Alhaji na gaji, na gaji da irin cin mutumcin da Sarai ke min a gidan nan, wai daga nasa k'afa na fita shikenan saina tarar da Sarai da Delu a gidan nan sunata cin nama na, a k'arshe ma dana musu magana kar ka so kaga rashin mutumcin da suka min ba, da nace kuma idan ka zo zan fad'a maka dan ka shiga tsakani na da ita, amma wai sai Sarai ta bud'a baki tace ai kai miji ne kawai ba ubangiji ba, dan haka baka da wuta ko aljannar da zaka sakata, dan haka ni kawai ka rama min cin mutumcin da ta min gaban k'awar ta." Wani huci yayi yace "Yanzu dama akan Saratu ne kike kuka haka? Me ya sa zaki tsaya ki bawa kanki wahala? Naga ai kina da damar dake kanki zaki hukunta ta ko bana nan, amma ba komai zata gae kurenta, wallahi zata san ta tab'a ki a gidan nan, yau zanga waya d'aure mata gindi a garin nan." Fitowa yayi daga d'akin ta biyo bayanshi tana ci gaba da rera kukan iskanci, shi kam d'akin shi ya shiga ya d'auko bulalar fata ya nufi d'akin Saratu da ita, suna zaune ita da Husseina saiko ya fad'o d'akin kamar an turo shi yana fad'in "Ina kike marar mutumci, har ni zaki wa fitsara a gida." Bai tsaya komai ba ya rufeta da duka da wannan bulalar, kamar yanda ta fad'awa yaran cewa babu ruwansu duk abinda suka ga mahaifinsu na mata, wannan dalilin ne ya tilastawa Hassana mik'ewa ta fito daga d'akin tana zubarda hawaye, karo ta ci da Ramma dake shirin shiga d'akin wanda yasa kafad'ar su ta had'u, kashe Hassana tayi da mari tana fad'in "Dan ubanki ni zaki bige? Ai bani nake dukan uwar taki ba, ubanki ne gashi nan idan zaki rama mata ne." D'auke hannunta tayi daga kunci ta rab'ata zata wuce Ramma ta sake cewa "Koda yake ma ai ba 'yan halak ta haifa ba shiyasa babu mai jin zafin abinda ake mata duk cikinku." Daf da k'ofar shigowa gidan ta tsaya tana kuka, cikin sand'a Husseina ta shigo dan kar kowa ya ji shigowarta, amma tana dosowa taji ihun mahaifiyar ta da gudu ta banko kai tana shirin zarcewa d'akin, da k'arfi Hassana ta rik'e ta gam tana fad'in "A'a Husseina, kinsan fa abinda Iyya ta fad'a mana, dan Allah ki barsu." Fizgewa tayi cikin zafin rai tana fad'in "Dallah malama ni sake ni, haka kawai muna ji muna gani saiya kashe mana uwa bayan ba wata tsiya yake tsinana mana ba." Sosai ta sake rik'e ta tace "To me zamuyi? Idan kin shiga zaki rama mata ne? Ko kuma zaki masa magana ne yaji? Kawai ki barshi idan ya gaji da dukanta ai zai dakata." Cikin b'acin rai da tafasar zuciya ta zauna k'asa dab'as ta fashe da kuka ita ma, kuma har lokacin Hassan bai daina dukanta ba har ta kai tayi shiru, suna haka cirko cirko suka ga ya fito daga d'akin yana ta bambami, Husseina kam da harara ta bishi ta mik'e suka shiga d'akin da gudu, zaune suka sameta rakub'e da bango sai shashek'a da take yi, kamar yanda suka saba Hassana ce ta rulgumota tana jijjigata tana fad'in "Kiyi hak'uri Iyya, kiyi hak'uri dan Allah komai zai zama tarihi wata rana." Suna haka kuma Suley ya shigo da sallama d'akin jiki a matuk'ar sanyaye sai ledar dake hannunshi, Hassana kad'ai ta amsa mishi kafin ya zauna gefensu ya mik'awa Husseina ledar hannunshi, sai lokacin Hassana tace "Suley kana lafiya? Na ganka kamar baka lafiya?" Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleta yace "Lafiya ta lau Hassana, na zo zan shigo ciki na ji hayaniya da sautin Iyya, shiyasa ban shigo ba tunda banga abinda zan iya yi ba." Husseina ce ta kalle shi tace "Wai har kaima dake namiji baka tab'a ji a zuciyarka ba kana so ka d'auki tsohon nan ka nunawa sama shi sannan ka sauke k'eyar shi k'asa? Gaskiya ni na fara gajiya." Kallonta yayi zaiyi magana Saratu ta mik'e saboda tuna abinda ya fad'a mata da zai fita cewa ta kai mi shi abincin shi yanzun nan, ganin ta fita ta bar musu d'akin yasa sukayi shiru kawai. Sai bayan kwana biyu Delu ta shirya tare da su Hassana suka tafi wajen malamin nan, shima kuma aradu Saratu ta tara da kai domin ba barinsu ake suna fita ba, haka Delu ta tafi dasu wajen malam Rabi'u, sam a ranta babu mummunan nufi sai na son taimaka musu, amma sai gashi tunda malamin ya d'ora idonshi akan Husseina sai yawunshi ya tsinke, ta wani fannin ya fad'a musu gaskiya kam da yace asiri ne aka musu dan kar suyi aure, ta wani b'angare kuma b'atar da su yayi da yace akwai maganin da zai bayar suyi aiki da shi amma dole Husseina ce zata dawo gobe ta karb'a, ba musu suka juyo suka dawo gidan, yau ma Hassana da Husseina shegen duka suka sha wajen Babansu saboda fitar da sukayi, amma hakan bai hanata komawa ba washe gari da magriba kamar yanda sukayi da malam, wannan zuwan kuma shine ya wargaza duk wani tanadi da tattali data jima tanawa kanta, duk yanda ta so bijere masa bai bata dama ba saboda ya nuna mata k'arfi, kuma tun farko ya riga daya ci galaba a kanta, a wannan zuwan ne malam rabi'u ya rabata da mutumcinta ta hanyar yin kaca-kaca da shi. Da k'yar ta kawo kanta gida tana kuka, amma kuma sai ta k'i yarda Saratu tasan abinda ya faru sai yar uwarta kad'ai abokiyar shawararta ta fad'a ma, Hassana ma ta shiga damuwa har ta kusa ta fita tashin hankali, amma haka suka dinga b'oyewa har lokaci ya dinga gangarawa, cikin hukuncin ubangiji kuma sai Allah ya fito musu da maza, d'aya d'an abokin Babansu ne yace yana son Hassana, sai wani mai mata biyu dake nan unguwarsu yace a bashi auren Husseina, dama mahaifinsu ya gaji dasu kamar yanda yake fad'a, dan haka ba'a d'auki lokaci ba aka d'aura musu aure kowace ta shiga d'akin aurenta. _K'alubalen har yanzu bai fara ba, yayin da *BADAK'ALAR* yanzu ne zata soma._ 😍 *See u guy's*😍 05/06/2020 à 20:36 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _12_ Zaha ta d'an shawarci mai gidan nata cewa ya za ayi aure haka kawai basu san waye shi ba, sannan ka d'auki 'ya ka bashi a sadaka, sanin dama sai anyi wannan cecekucen yasa yace shi zai yi wa 'yarshi duk wani abu da akewa kowace yar gata, haka lokacin ya ya fara tafiya dama kuma ba wani lokaci bane mai tsayi, har lokacin Zeeya da suley basu had'u ba dan k'iyayyarshi ce zalla a zuciyarta, shi kuma bai ma san ainihin me yake ji a game da ita ba, ana haka juma'a ta zo kuma aka d'aura aure, inda Alghabit ya wa suley wakilci liman kuma ya wa Zeeya, sadaki mafi girma da daraja ya biya wanda sai wane da wane, duk wata al'ada saida akayi ba'a bar komai ba, kafin nan amarya ta tare ita da halinta. Zaman *doya* da *manja* suka fara, Zeeya dai banda gori da rashin kunya babu abinda take wa Suley, kullum ita ce fad'in bashi da kowa bashi da komai, da dukiyar ubanta yake duk wani abu na rayuwa, tunda sukayi aure basu kwana d'aki d'aya ba, dan lokacin shigowarshi nayi zata rufe na ta d'akin, abunci kam dama iya bakinta take dafawa, Suley yasha wahalar Zeeya fiye da tunanin mai karatu. Ni kaina da ana bani labari na yaba da hak'urin shi, dan kad'an daga iskancin Zeeya yana iya d'iban ruwan wanka ta zubar da gangan ko kuma ta zuba wasu ruwan masu datti a ciki, ko kuma ta d'ibi k'asa ta zuba, ya kan shiga wanka ya rataya kayanshi a katanga da gangan ta d'auke kayan ta musu shark'af da ruwa, ankai matakin da saida Zeeya ta d'auki kayan Suley masu kyau wanda yake fita da shi tasa sabuwar wuk'a ta yagasu, Zeeya na iya ganin Suley zaune yana alwala ta d'auki sharar iskanci ta dinga bad'a mishi k'ura a jiki, wallahi wallahi yanda mai bani labarin ta fad'a min tace duk wannan iskancin idan tayi sai dai ya kalleta ya girgiza kai yace "Allah ya kyauta, ya ganar da ke gaskiya." *Bayan wata d'aya* ya shirya tafiya gida dan ganin me ake ciki tunda yanzu Allah ya hore mishi kud'in mota harda ma na guzuri da tsaraba, haka ya sa kai ya tafi Zeeya bata damu ba dan dama nesa take so suyi da juna, bayan yaje ne ya samu labarin rasuwar mahaifiyarshi da ita kad'ai ta rage mi shi, hakan yasa shi dasa nashi kukan harya gode Allah, abin duniya ne ya taru ya mishi yawa, ga rashin uwa ga rashin sanin inda Husseina take, dan har yanzu babu wanda yace ya ganta da idon shi, haka Hassana ta bashi labarin rabon gadon da akayi tare da nuna masa yan dabbobin da aka basu, hakan ya b'ata mi shi rai sosai ta yanda har ya fara ikrarin cewa sai an sake wannan rabon gadon, dan son zuciya yayi yawa cikin wanda akayi, kuka sosai Hassana ta dinga yi tace yayi hak'uri kawai ya share ya barwa Allah, tunda gashi a cikin watannin da basu kai shekara ba har sun had'a garke, haka ya hak'ura badan ya so ba ita kuma tasan ko yanzu sai wani abun ya faru idan yayi maganar, haka ya shirya sake komawa wajen iyalinshi cike da burin son zama a mahaifarshi, sai dai abu d'aya ba zai yiwu lokaci d'aya haka yace zai dawo da Zeeya garin nan ba a yanda take, dan haka ya shirya ya shirya ya tafi ya kuma ce Hassana ta ci gaba da saka ido wajen neman yer uwarsu, idan an samu labari to taje kasuwa ta samu fatake dake yawon fatauci har zuwa Agadez ta bayar da sak'o za'a sanar da shi, sannan ta ci gaba da kula da duka gadon na su, haka ya koma ya samu Zeeya suka d'ora daga inda aka tsaya. *Wata shida* suka d'auka a haka kafin ta fara kunno masa wutar saiya saketa, ita a dole ta gaji da zama da shi saiya saketa, shi kuma ya fad'a mata abinda ba zai iya ba kenan saboda darajar mahaifinta a wurinshi, duk dan tasa ya saketa saita fara fita barkatai ba tare da saninshi ba, idan ta fita har ta kan iya kai dare bata dawo ba, idan ya tambaye ta daga ina kike sai dai tace "Daga wajen wanda zuciya ta ke so, idan kuma kana da zuciya ka sakeni tun kafin na kawo maka cikin da baka da iko a kan shi." Girgiza kai kawai yake yace "Allah ya kyauta, ya ganar dake gaskiya." "Ya dai ganar da kai, dan kaine ke k'in gaskiya kake rufe ido ma idan ka ganta, na fad'a maka ya fi yawan gashin rak'umi cewa vana sonka, amma ka k'i rabuwa da ni na huta kaima ka huta." Haka abubuwa ke tafiya ba dad'in yau bare na gobe, kuma duk fitar da take babu inda take zuwa, daga gidan 'yan uwa sai abokai, duk da bata da ilimin addini da kuma sanin yakamata, amma tasan zina da aure babban bala'i ne, shiyasa bata sake zina ba tunda sukayi aure, ana hakane har ranar dai ta ji tana buk'atar kusanci da namiji, tun safiyar ranar Suley ya ga banbanci, daga yanda take lumshe ido tana kallonshi, murya k'asa k'asa cikin wani irin yanayi, rigar dake jikinta ta matseta sosai ta fito mata da komai, haka shi dai ya fice ya barta dan baisan me hakan ke nufi ba baima fahimci meye damuwar ba, yana fita taji haushi sosai inda tasa hannunta tana ta shafar k'irjin ta da take jin yana mata k'yaik'ayi, haka ta wuni ba kuzari har lokacin dawowar Suley, dole ta yanke shawarar tunkararshi da kanta, ya dawo kamar yanda ya saba ya shiga wanka bayan ya aje kayanshi inda ba zata iya gani ba bare ta d'auka, tsaf ya gama ya saka kayanshi, saida ya fara lek'owa dan tunanin kar azo ta fara sharar nan ta rashin gaba, jin shiru yasa ya k'arasa fitowa gaba d'aya, mamakin rashin ganinta yake a tsakar gidan har yayi gaggawar shigewa d'akin shi ya maida k'ofa ya rufe, juyawar da zaiyi sai ko Zeeya zaune bakin gadonshi na k'arfe, gabanshi ne ya shiga fad'uwa ta ko ina yana kallon hannayenta kar azo da makami take, tasowa tayi ta nufo shi ta fara shafashi, ido ya zaro yana kallonta yace "Zeeya'atu kasheni zakiyi?" Cike da salo na yan duniya tace "Kai ne dai zaka kasheni idan baka kulani ba." Hannunshi ta kamo ta d'ora tafin hannunshi akan nononta na b'angaren dama, tana jin haka ta wani lumshe ido tare da zage rigar tayi k'asa, shi kam yana jin babu rigar da tayi shamaki saiya rufe ido yace "Sallalahu sanyi k'alau." 😂😂😂 *Maganar fa babbace domin kuwa harkace wannan ta kakanninmu* Sai wannan rana ce Suley yasan da wannan duniyar dake b'oye jikin kowace mace, a wannan rana ce yayi dana sanin k'in zuwa tun da wuri, musamman da Zeeya ta zage ta nuna mishi ita fa 'yar barikin gida ce, sam mantawa yayi a wannan lokacin saida ya samu nutsuwa ya tuna da hakan, ita kanta Zeeya ta yaba da namijin k'ok'arin shi, dan inhar zata fad'i gaskiya to ya zo mata yanda take burin azo mata, buk'atar ta na biya ta koma Zeeyar ta ta asali, ta sake fito da salon rashin mutumci iri iri, *sati* uku babu wani abinda ya sake shiga tsakaninsu saida Suley yaji ya kai mak'ura ba zai iya hak'ura ba ya sameta har d'akin ta ya labb'eta, amma sai cewa tayi idan har yana so ta yarda saiya siyo mata gasashen nama na bakin kasuwa, tasan tafiya ce mai nisa amma haka ya daure ya je ya kawo, duk da haka saida ta gama wainashi taga kamar zai mata kuka kafin tayi wanka ta fito ta kwanta kan gado ta wani kalleshi tace "To taho." _Sai kace zaki bawa yaro nono._ Jiki na rawa ya haura kan gado, tashi tayi zaune cikin tsawa tace "To ni ce zan cire maka kayan?" Saukowa ya sakeyi daga kan gado ya cire kayan zai sake haurawa tace "Kaga muje ma d'akin ka, na fasa anan d'in." Haka yabi bayanta bawan Allah shi dai ya samu nutsuwa kawai, a d'akin nashi ma saida taji yana daf da shiga ta zabura ta tashi zaune tace "Kaga ruwa nake so nasha, duk naman nan ya tsaya min a k'irji." "To, to bara na kawo miki." Ya fad'a yana barin d'akin bai ko da nutsuwar da zaisan babu kaya a jikinshi, da irin wannan iskancin ta dinga ja masa rai, har saida ya shiga ya fara kenan ta sake yakice shi daga jikinta tace ya isa haka ta gaji, da sauri ya durko k'asa ya rik'e k'afar ta yace "Ki wa Allah Zeeya kiyi hak'uri, wallahi ba zan iya ba, ki fad'i duk abinda kike so ni kuma zan miki shi." Ba tausayi ta mik'e ta d'auki zaninta tayi d'aurin k'irji ta nufi k'ofar fita, wani takaici ne ya rufe shi dan tunaninshi d'aya ne akwai abinda ta mishi tun waccen ranar shiyasa yake jin haka, hannunta ya fincikota ta fad'a kan gadon ya bita ya haye, zata tureshi ya rik'e hannayen nata ya matseta d'aya hannunshi kuma ya rufe mata baki sosai yace "Wallahi duk abinda kika min sai dai ya k'are kanki, ina zamana lafiya kika tsokano ni." Haka ya janye zanin nata ya bud'e k'afafun ta ya danna kanshi ciki, lilis ya mata dan bai tausaya mata ba ko kad'an saboda takaicinta da yake da shi, ita kanta tasan ta shiga uku a ranar, dan bata tab'a tsalmanin irin haka ba, tunda wannan abu ya faru Zeeya ta sake tsanarshi, zagin yau daban na gobe daban, duk wata mummunar kalma bata jin nauyi ko kunyar fad'a mishi ita, kullum saita mishi gorin daga ta lasa mishi zuma shine zai zama jarababbe, mugu azzalumi, macuci, wannan kalmomin kam tamkar sawar albarka ne a wurinta, tun ranshina b'aci yana tunanin ya fad'a mata shi fa yasan komai har ya kai ma baya son tona mata asirin, haka rayuwar ta ci gaba da gungura musu har lokacin da Allah ta mishi baiwar gane Zeeya na da ciki tun ita bata fahimta ba, kuma ya gane ne daga yanda kwana biyu ko kallonshi ba tayi bare tayi masifa da bala'in data saba, sai yawon tsargin yawu da take ga kuma kyawu data k'ara, duk da ta tab'a d'aukar ciki amma saita kasa ganewa da wuri cewa ciki ne da ita, yau ma kamar kwana biyu da suka gabata tana zaune k'ofar d'akinta tunda safe ya fito zai fita, kallonta yake sosai ganin kwanon d'umame a gaban ta amma ta kasa ci sai yamutsar fuska take tana tofar da yawu, karo na farko a zamanshi da ita da ya ji wani abu ya bugi zuciyarshi a game da ita tare da jin wani mugun tausayinta ya kama shi, dan a iya fahimtar da yayi mata ya fahimci tana son cin d'umamen tuwo musamman ma miyar kuka, dakewa yayi yana murmushi yace "Ni zan fita, me kike so na taho miki da shi ne? Tunda na ga baki son cin tuwon." A zatonshi zata taso mishi ne kamar yanda ta saba cikin wannan muryarta ta data zama zazzak'a a kunnenshi, amma sai tace cikin ruwan sanyi "Ina ruwanka da matsalata to, kaje kayi abinda ke gabanka malam." Cikin wani yanayi yace "Taya zan iya kallonki a haka baki ci komai ba, bayan kuma bake kad'ai bace." "Ban gane bani kad'ai bace? Mu nawa ka gani anan? Kaga malam dan Allah ka fita ka bani wuri ko, wallahi na tsaneka ban son ganinka kusa da ni." Murmushi ya mata yace "Ashe da ido na zanga ranar da Zeeya'atu take gajiya da surfa tijara, to shikenan idan na fita na siyo miki tsire sai na zo na kawo miki, dan bana barki da yunwa ba alhalin kina da juna biyu." Yana fad'a ya sa kai ya fita, sosai ta girgiza da jin wai ciki ne da ita, ai sai ta kasa zaune ta kasa tsaye, sam tana ji ba zata iya yarda ta haihu da Suley ba, dan haka ta canza kayanta ta nufi gidansu, da shigarta mahaifinta ta fara cin karo da shi zai fita shima, da mamaki ya tambayeta "Zeeya'atu lafiya na ganki da safiya haka?" Cike da girmamawa tace " Lafiya k'alau Baa, na zo ganinku ne dama." "Amma a safiyar nan? Ina mijin naki yake?" "Baa ai tare muke da shi ma ya wuce kasuwa, yace na zauna zuwa yamma saina koma." Fita yayi ita kuma ta shiga ciki, nan a mahaifiyarta ta samu sai dai bata fad'a ata meya kawota ba, dan tasan ba lallai ta yarda da abinda ya kawotan ba, duk da tana goya mata baya amma wannan karan tasan zasu iya samun matsala, dan haka taja baki tayi shiru amma ta saka ido kowane lungu da sak'o na gidan da tasan mahaifiyarta na ajiya, kusan wuni tayi a gidan kafin tayi nasarar ganin k'ullin maganin da suka je suka amso wajen wani mai maganin gargajiya na zubar da ciki, d'auka tayi ba jimawa kuma tace ta tafi gida, tana zuwa bata tsaya komai ba ta jik'a maganin kamar yanda sukayi waccen lokacin tasha, baifi awa d'aya ba cikinta ya fara matsanancin ciwo, lokaci d'aya ta fita hayyacinta kamar ba ita ba, ana haka kuma jini ya biyo baya ya fara mata zuba, Suley ne ya shigo da sallama amma jin ihunta yasa ya hanzarta lek'awa d'akin nata, k'arasawa yayi yana tambayarta lafiya, amma ta kasa magana sai matsar ciki take, tunawa da yayi yanayin daya ganta waccen ranar da kuma tunawa da yayi tana da ciki, ranar farko da ranshi ya b'ace fiye da kima a kan Zeeya wanda har yasa shi zabgeta da mari duk da halin da take ciki, kamar zaiyi kuka yace "Yanzu Zeeya'atu cikin nawa ne zaki zubar? Cikin da muka samu ta hanyar sunna?" Shiru yayi yana tattara nutsuwarshi kafin ya juyo ya kalleta yace "Insha Allahu indai wannan cikin na halak ne wallahi babu abinda zai same shi, ba zai zube ba Zeeya'atu saiya fito duniyako ba kya so." Hak'ik'a a duniya akwai bayin da Allah ke musu baiwa ta hanyoyi daban daban, Zeeya'atu kam tasha wahala a banza dan kuwa cikin nan bai zube ba, zan iya kiran haka da dama Allah ya rubuta cikin nan zai rayu kuma zai fito ya taka k'asa, ko kuma na ce Suley bawan Allah ne wanda Allah ya kub'utar da rantsuwarshi saboda kar kaffara ta hau kanshi, (duk hakan mai yiwa ne a wajen ubangiji), saida akayi tafiya mai nisa aka kaita babban asibiti, jini aka k'ara mata tare da cewa a kiyaye gaba, daga haka kuma ta fara rainon cikin, sai kuma sabbin rashin mutumcin data fito da su kala kala, amma sai Suley ya sake banza da ita yana shanyewa kamar yanda ya shanye na baya. Yau ma kamar kullum daga d'akin shi ya fito cikin shirin fita, ya rufe k'ofa ya juyo kenan kamar saukar ruwan sama sai ko yaji ruwa a jikinshi, saida numfashinshi ya sauke na wucen gadi dan sosai ruwan suka dira a fuskarshi, kusan minti biyu yayi a haka kafin ya bud'e ido ya sauke akan Zeeya dake gabanshi da robar wanke-wanke ita ma tana kallonshi, a hankali ya fara kallon jikinshi ba wai jik'ewa kad'ai kayanshi sukayi ba harda datti na abinci duka, sake kallonta yayi wata zuciya na fad'a mishi yi mata shegen duka gobe ba zata sake ba, amma yana kai kallonshi kan tulelen cikinta da yanzu yake wata na bakwai sai kawai yaji ya k'ak'aro wani murmushin da ganin kasan na bak'in ciki ne, girgiza kai yayi yace " Ke ba shed'an bace Zeeya, dan haka baki fi k'arfin addu'a ba, duk da nasan komai a kanki wanda ba kya tunanin na sani, amma ina miki fatan shiriya saboda ina so na zauna dake cikin aminci ko dan hallacin da mahaifinki ya min a rayuwa, dan haka kije Allah ya shiryeki shirin addinin musulunci, Allah ya ganar dake gaskiya." Cikin sanyin jiki ya cire rigarshi ya shanyata a zanar data shiga tsakanin filin gidan da k'ofar shigowa, d'aki ya koma ya sake kaya ya fito ita kuma ta ci gaba da kai da kawonta , saida taga harya kusa kaiwa k'ofa tace "Ni idan ka fita ka siyo min masara ina so zan dafa." Juyowa yayi ya kalleta yace "To, zan siyo miki." To fa da irin wannan wulak'ancin suke zaune, duk da dai an samu canji ta b'angaren zuciyar Zeeya, amma a halinta kam babu abinda ya sauya, *kwana tashi* a haka har Allah ya sauki Zeeya lafiya, ta haihu kuma haihuwa ta ban mamaki a waccen lokacin, domin kuwa *'yan uku* haka ta haifesu kuma duka maza, ba mutane a kad'ai har gwamnati saida ta shiga lamarin yaran nan ta hanyar basu kyauta da kuma iyayensu, yara sun zo da arzik'i dayawa, dan bayan kyautar da gwamnati ta musu har sarkin garin agadez mai zamani a wannan lokacin saida ya musu goma ta arzik'i, masha Allahu yaea sun ci sunan *Hassan*, *Hussein*, da kuma *Harouna* (wanda suke kiranshi da *Gambo*), duk abubuwan da Zeeya tayi a baya Suley ya manta da su ya kuma mata uzuri, gashi tunda ta haihu abubuwa sunyi sauk'i saboda kakarta da kuma k'anwar ta *Fatime* suke zaune a gidan tare da ita, Fatime yarinya ce mai nutsuwa da kunya, dan ko ido bata had'awa da Suley bare wasa ya shiga tsakaninsu, har tayi arba'in suna tare da ita saboda rainon yaya uku da wahala sosai, ganin idon mutane yasa Zeeya ziyartar d'akin Suley idan dare yayi, yanzu kam sai ladabi da take mishi idan gaban mutane ne amma bayan idonsu kuma halin take siyarwa, a haka wata rana ta shiga d'akin na shi ya nemi hakk'in shi wurinta amma ta zazzaga masa bala'i son ranta, har da cewa ba zata yarda wani abu ya sake shiga tsakaninsu ba bare harta sake haihuwa dashi, murmushi ya mata yace "Kuma gashi kam an fad'a mana a tarihin gidanmu muna da baiwar haihuwar 'yan bibbiyu, sai gashi ke kin fara da uku abun birgewa, mahaifina ma yana da Husseini, sannan k'annai na ma yan biyu ne." Rana ta farko data fara sanin yana da yan uwa, amma bata nuna wani damuwa ba, zaune yayi a lokacin sosai yana kallonta yace "Zeeya'atu, a k'alla yanzu muna da shekara d'aya da rabi da aure, a wannan lokacin zan iya cewa ni dake bamuyi farin ciki ba, Zeeya kinyi min abubuwa da dama a gidan nan daya kamata ace na d'auki mataki akan haka, amma ban d'auka ba saboda mahaifinki ya min komai a rayuwa, amma daga ranar da kika haifo min yaran nan, na kallesu da idona na kuma tuna wahalar da kika sha wajen haihuwarsu, sai naji kin samu wani girma da matsayi a zuciyata, Zeeya'atu duk da kin k'untata min a rayuwa amma sai naji a duk duniyar nan babu mai so na da k'aunata sama dake, zee'ayatu matsololin rayuwa da muka shiga ne harya jefoni garinku, banda kowa sai yan uwa na mata biyu, wanda har yanzu d'aya daga ciki bansan ina take ba, amma sai gashi lokaci d'aya kin haifo min magada yara maza har uku..." Rawarda muryarshi takeyi ne yasa yayi shiru ya duk'ar da kanshi, hawaye ne suka dinga zarya a fuskarshi, hakan ne yasa Zeeya jin wani abu a zuciyarta da bata tab'a ji a game dashi ba sai yau, ji take kamar ta tashi ta rarrasheshi amma kuma tana jin ba girmanta bane, saida ya gaji dan kanshi ya share hawayenshiya d'ago ya ci gaba da cewa "Tabbas kyautar daga Allah take, amma kema kinyi k'ok'ari Zeeya, ina godiya sosai ga Allah daya bani su, sannan kema ina gode miki, Allah ya saka miki da alkairinsa, Allah ya baki lafiyar da zaki shayar dasu cikin k'oshin lafiya." Hak'ik'a maganganunshi Sun huda zuciyarta sosai ta yanda ta kasa ko motsin kirki harya fita daga d'akin, haka aka ci gaba da tafiya duk da Zeeya na jin soyayyar mijin nata amma babu abinda ta rage a game da rashin mutumci, a haka yara sukayi wata uku da haihuwa, zuwa lokacin kuma kakarta ta koma sai Fatime ke tayata kula da yaran, ana haka Suley ya shirya sake komawa ganin iyalinshi, ya so tafiya tare da Zeeya dan taga mahaifarshi ko ya tsira daga gorin da take masa, amma sai Zeeya tace ai babu inda zataje tunda babu wanda ta sani, haka yayi ban kwana dasu ya kuma bar musu duk abin buk'ata sannan ya kama hanya. *Allah ka mana kyakyawan k'arshe.* 😍 06/06/2020 à 12:38 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _11_ Husseina dai dama ba nisa akayi da ita ba daga gidan iyayen ta, dan daga gidan ana hangen gidan nata iyayenta, sai dai kuma a wannan rana taga tashin hankalin da bata tab'a gani ba a tsawon rayuwarta, dan wannan daren nata na farko daren tonon asiri da tashin hankali ya zamar mata, sam *Salisou* bai mata da kyau ba a wannan rana ko nace dare, domin kuwa dukan mutuwa ya mata tare da yi mata saki har uku, daga shi har ita da sauran matanshi babu wanda yayi bacci, kumfar baki kawai yake yana fad'in shi taimakonsu ne yayi ya aureta saboda ganin ta jima babu aure, ashe dai da dalili shiyasa basu samu miji ba, tunda gudun-gudun safiya ya shiga gidan mahaifiyarshi dake had'e da nashi gidan, kaf ya kwashe ya fad'a mata abinda ke faruwa, nan fa ita ma ta d'ora ta ta kalar tijarar tana sababi, abinka ga sanyin safiya da sannan duk wanda yasan unguwar d'an gulbi yasan unguwa ce da babu sarari sosai, hakan yasa kowa kamar har gidanshi akaje aka fad'a mishi saboda yanda mutane dayawa suka fito kallon k'wam, kamar a tatsuniya haka Salisou da uwarshi suka dinga watso yan kayan da aka kaiwa Husseina wacce ita kanta suka turo k'eyar ta waje, banda kuka babu abinda take kamar zata had'e zuciya ta mutu, ga shegen dukan daya mata wanda yasa jikinta yin tsami. Labari ne ya samu mutanen gidansu suma suka fito dan jin ance da Husseina abin ke faruwa, a lokacin tana tafiya a hankali zata zo gidansu, tana zuwa k'ofar gidan Hassan ya tare k'ofa yace "Gidan nan kike nufin shiga? Ai in kinga haka ta faru to babu raina ne, dan haka tun wuri ma kisan inda dare ya miki, dan ni ba'a zina aka haife bi ba kuma duk zuri'ar mu babu mazinaci, dan haka wallahi ba zan haifi karuwa a gidana ba." Ramma dake daga cikin soro ce tace "Alhaji haihuwar karuwa na nawa kuma, ai sai dai kar a k'ara, amma kam ka riga daka haifeta." "Ai kuwa ba dai a gidan nan ba wallahi." Ya fad'a lokaci d'aya ya kalli Husseina da banda kuka babu abinda take yace "Zaki b'ace min da gani ko sai ci uwarki a wurin nan, k'ur'ani ba zaki shiga gidan nan ba, idan kuma uwarki ce ke saki duk iskancin to ki fad'a min saina turo miki ita ku tafi tare." Zubewa tayi kan gwiwoyinta cikin tsananin kuka ta had'e hannayenta tace "Dan Allah Baba, dan annabi, ka dubi girman Allah ka barni na shiga ciki, Baba bana da inda zanje idan na bar nan." "To ni ina ruwa na, wannan matsalarki ce ba tawa ba, da da kike iskancin baki tuna da irin wannan ranar ba." Saratu na k'ofar d'akin ta tana hango duk abinda ke faruwa daga nan, kuka take tana addu'a tare da tunanin yanda akayi haka ta faru, tana cikin wannan tunani ne ta sake jin ihun Husseina wacce Ramma ta sake mik'owa Hassan wani ice daga nan soron wanda ake ajewa saboda lokacin damuna ya fara jibgarta a filin Allah yana fad'in "Kije ki yi karuwanci mana, wannan keta shafa bani ba, dama karuwar gida ce bamu sani bane." Lokacin ne Saratu ta fito tana kuka tana bashi hak'uri, amma a k'arshe sai yace ta zab'a ko zama dashi ko da 'yarta, bud'ar bakin Saratu cewa tayi "Ita fa 'yata ce data fito daga jikina, ko ka manta da karin maganar nan da ake cewa *namiji goma ba uba goma bane*? Zanyi farin cikin k'arar da rayuwata a tare da 'ya'yana, dan haka na zab'i na tafi tare da ita duk inda zata saka k'afa." Kama Husseina tayi amma saita sake sulalewa tana kuka tace "A'a Inna, ban cancanci ki ruguza rayuwar aurenki ba a kaina, shekararku talatin da hud'u tare, ba zan yarda yau na zama silar wargajewarshi ba, komai daya faru laifina ne." "Nima kuma ba zan tab'a bari taki rayuwar ta lalace ba, dan ni tawa rayuwar dama ta jima da gurb'acewa tunda na shigo gidan mahaifinku, dan haka ba zan tab'a barinki ke kad'ai ba bayan bansan ina zaki je ba." Hannayenta ta rik'e sosai tace "Inna kiyi hak'uri ki barni na tafi, na miki alk'awarin kare mutumci na, sannan zan dawo nan bada jimawa ba, Inna yanzu ran Baba a b'ace yake, zuwa lokacin da zai huce zan dawo nasan zai karb'e ni." Sun jima suna wannan musayar yawun kafin Husseina ta saki hannunta ta fara tafiya, za tabi bayanta Hassan yace idan har ta tafi bada yawunshi ba Allah ya isa, juyowa Husseina tayi taga tabbas mahaifiyarta fa idonta sun rufe, hakan yasa ta kalli gabanta ta ari na kare da gudu ta ratsa mutanen dake kallonsu ta bar wurin, saboda a lokacin akwai kula da hakk'in mak'wabtaka yasa wani mak'wabcinsu ne ya bi bayanta ya tafi da ita gidanshi. Kwanan Husseina *takwas* a gidan nan babu wata matsala, babu wani abu da mutanen gidan ke nuna mata na k'yama ko banbanci, duk da Saratu bata zo ta ganta ba saboda tun ranar da abun nan ya faru doka mai tsanani Hassan ya kafa mata, wanda yanzu ko abincin gidan baya bata sai Suley ne idan yayi fafutuka yake kawo mata, sai Suley ne ke ziyartar Husseina yaga halin da take ciki, haka ma yar uwarta Hassana ta zo ta ganta, ana haka kuma sai wata matsalar ta kunno kai, domin kuwa ciki ne ya bayyana jikin Husseina, bayan ta tabbatarwa da kanta tana da ciki shigar wasu watanni da suka gabata sai kawai ta yanke hukunci a kai, da asuba ta bar gidan *malam Yacub* ta shiga gari, dan a tunaninta bata da ciki ma aka wulak'anta ta bare yanzu asan tana da cikin banzan malamin nan. Yawo take babu wurin zuwa, wanda a lokacin kud'in mota kawai take nema da zai kaita Diffa wajen dangin mahaifiyarta komai rashin dad'in can d'in zaifi mata, amma sai gashi har magriba ta mata bata ma samu abinda zata saka a bakinta ba, dan duk wanda ta nema taimako sai an mata kallon tsaf, ganinta zaune da kyau tsaye da kyau amma tana neman taimako dan mutuwar zuciya, dan haka babu wanda yayi yunk'urin taimaka mata, tana cikin yawo ta had'u da wani babban mutum ta nemi taimakonshi, amma saiya nuna mata idan ita ma zata taimaka masa saiya taimaka har da wurin kwana ma, mik'ewa tayi daga durk'ushin da tayi ta juya baya zata tafi, hawaye ne suka fara mata zarya a ido inda kalmar mahaifinta ke dawo mata a k'wak'walwa ta cewa " *Kije kiyi karuwanci mana*, wannan ke ta shafa bani ba, dama karuwar gida ce ke bamu sani bane." Wannan maganar ita ta tsaya mata a rai sosai inda shed'an kuma ya rad'a mata tashi hud'ubar a kunne, juyowa tayi da sauri wajen mutumin ta same shi yana shirin tashin motonshi, tana zuwa yace "Ke ya dai, me kika dawo yi?" "Na yarda." Abinda ta fad'a kenan, kuma wannan kalmar ita ce duk wani makulli na ruguza rayuwarta, shi dai dama d'an tasha ne na gaske, yana d'aukarta daga nan wata unguwa ya nufa da ita inda matattara yan bariki ne, *kara*, wani fili ne da duk wata karuwa ko karuwi😂 ke zama anan, suna zuwa ya abka da ita wata bukka dan dama ba d'akunan basa wuce na kara, saida ya fara cika mata cikinta da gasasshen nama tasha ruwan rada sannan sukayi abinda ya kawo, farkon al'amarin Husseina taji wani iri da ita ga matuk'ar kunya data hanata katab'us, amma bayan komai ya kammala ta kalleshi take shed'an ya cire mata duk wata kunyar da take da ita. Malam Yacub da suley ne suka shiga nemanta amma shiru, bai ma yarda Saratu tasan bata nan ba har saida aka kwashe kwana biyar, tunda ya sanar da ita ta tashi hankalinta, a lokacin ne fa duk wasu tsofaffin ciwuna da take fama da su wanda basu bayyana sai suka fara bayyana, sosai take jin jiki Suley kuma na fama da k'ok'ari wajen samar mata magani na gargajiya, *ba'a rabu da Bukar ba an haifi Abu*, Alhaji Hassan shima saiya samu had'ari a hanyarshi ta zuwa kasuwa, gawarshi kawai aka dawo da ita gidan, tashin hankalin da suka gani a ranar bai misaltuwa, duk k'ok'arin Suley na ganin mahaifiyarshi bata san halin da ake ciki ba abun ya ci tura, dan koke-koken Ramma da yayanta Barira da Rahmatu shiyasa tasan meke faruwa, nan ita ma jiki ya yamutse aka gaza gane kanta. Tsawon kwana sha hud'u d'in da akayi na rasuwar Alhaji Hassan Saratu bata san me ake yi ba, saida mak'wabtan su suka taimaka aka kaita asibiti, jinya take sosai inda ake kula da ita a asibiti, wasa wasa sai gashi ta kwashe sati biyu a asibitin, bayan an sallamota kuma sun dawo gida da kwana shida akayi wa Hassan sadakar arba'in. A ranar kuma a gaban mutane Ramma ta nemi yan uwan Hassan da maganar a raba gado tunda anyi arba'in, duk da abun bai ma kowa dad'i ba amma dayake ta riga data dasa musu shakkunta a zuciyarsu yasa suka amince da maganar, bayan kwana biyu da faruwar hakan Ramma ta yiwa Suley kurciya ya bar gida gaba d'aya, wayar gari akayi babu shi babu dalilinshi, abun bai tashi hankalin saratu ba saida aka kwashe kwana uku, a haka kuma Ramma ta tilasta aka raba gado duk da a lokacin akwai k'arancin ilimin addini, an raba gado yayanta sun samu rabonsu inda saratu aka bata abinda ko kashi d'aya na mace d'aya bai kai ba, wannan bak'in cikin da k'uncin yasa Saratu ita ma cewa ga garinku nan, haka ita ma akayi na ta makokin inda abinda aka basu ya zama k'ark'ashin kulawar Hassana. *Duk* abin nan dake faruwa Husseina na cikin garin, inda gaba d'aya ta lalace ta zama karuwa mai lasisi, duk da ba kowane lokaci take zaune garin maradi ba, dan wasu lokuta mawak'a suna d'aukarsu su tafi dasu wani gari dake nigeria da ake kira *hirji*, cikin jikinta kuma magajiya uwar karuwai ta so a zubar dashi amma tace a'a, da haka ta dinga rainon cikin kusan a wannan lokacin ita ce karuwar da wasu suka fi nema suna bayar da kud'i masu yawa dan su kwanta da ita saboda tana da ciki, saida cikinta ya tsufa ta aje harkar na d'an lokaci har saida ta haihu, namiji ta haifa wanda mata masu zaman kansu sukayi babban bidiri, mawak'a suka baje nasu kolin daga ciki harda irinsu margayi *Sa'adou bori*, ranar suna an kwana ana cashewa daga k'arshe dai yaro ya ci sunan *Labaran* a cewar Husseina shi yafi kowa bawa gidan karuwan tallafi, dan haka ya cancanci a mishi takwara, (duk wannan fa abun ya faru),duk da a lokacin ta samu labarin mutuwar mahaifinta amma sai tace "Allah raka taki gona." Rasuwar mahaifiyarta kad'ai ta girgiza ta data samu labari, amma duk da haka bata je gidan ba saboda tace bata son sake ganin unguwar ma, haka ma wajen Suley tafiya kawai yake yi, yunwa na ci k'ishin ruwa na ci, domin duk abinda yake samu yasa a cikinshi ba isarshi yake ba, hasalima ba komai ne yake samu mai kyau ya ci ba, haka yake tafiya ba um ba um um, ya galabaita sosai ya jikkata ta yanda ya fita hayyacinshi, haka Suley ya d'auki tsawon lokaci yana tafiya ba tare da yasan inda yake saka k'afar sa ba har tsawon *wata biyu*, a cikin tafiyarshi ne Allah ya had'a shi da wani mutum mai kirki d'an kasuwa mai sunan *Alghabit*, mutumin *Agadez* ne kuma hamshak'in mai kud'i, yana kan rak'uminshi ya ga Suley na tafiya kamar gunki, kallo d'aya ya masa ya tabbatar yana tare da k'ishin ruwa da kuma yunwa dama gajiya, dan kuwa har k'afafun shi sun kumbura kamar na mai tsohon ciki saboda tafiya, tsayar da rak'umin yayi dan a wannan lokacin shine abun hawan kuma mai daraja garesu, duk da akwai mota a lokacin amma dai bata damesu ba kamar rak'umi ko kuma moto, saida rak'umin ya durk'usa har k'asa ya sauka ya tunkari Suley, tare gabanshi yayi yana mishi magana da gurb'atacciyar hausarshi daya d'an kama wajen yawon kasuwancinshi a bakin hausawan, ganin kallonshi kawai yake ya tabbatar ba lafiya yake ba, hannunshi ya kamo ya zo kusa da rak'uminshi ya d'auki aglami (buzun sallah) da gorar ruwa da kuma wani d'aurin abu a cikin fata, gefe suka koma k'ark'ashin wata bishiya ya shinfid'a aglamin ya zaunar da Suley, ruwan ya fara bashi ai ko da sauri ya fizga daga hannunshi ya kifa baki bai sauke ba saida ya shanye, da mamaki da kuma tausayinshi ya zauna kusa da shi ya bud'e wannan d'aurin ashe akushi ne a ciki da abinci, nan ma abincin nan ya ci sosai kafin ya sake bulbulo mishi ruwa a yar babbar jarkar da ke d'aure da rak'umin. Tare ya tafi da shi a d'ora shi akan rak'umin, idan dare yayi su yada zango da safe su ci gaba, kwana goma sha bakwai suka d'auka kafin suka isa garin agadez. *A garguje* Haka ya sauke Suley gidanshi da taimakon iyalinshi, inda ya samu limamin unguwarsu ya zo da shi har gidan ya nuna mishi Suley, daga lokacin aka d'ora shi akan magani da rok'on Allah, Allah maji rok'on bayinsa sai gashi cikin *wata biyu* Suley ya samu lafiya ya dawo kamar yanda yake, Alghabit dama 'ya'yanshi mata ne suka fi yawa, dan haka saiya rik'e Suley kamar d'an daya haifa, tunda jiki yayi kyau sai Suley ya d'aura d'amarar neman kud'i dan yaje ga ahlinshi ya tallafesu, hakan yasa duk safe ta Allah ya kan shirya ya fita kasuwa, lokuta da dama dakon kayan mutane yake ana biyanshi kud'i kad'an, wani lokacin kuma idan kayan manyan yan kasuwa sun zo sai su sauke kayan a biyasu, da irin wannan k'ok'arin na shi ya fara tara kud'in komawa gida, duk lokacin da zai fita idan Alghabit ya tambayeshi sai yace zaije zaga gari ne kawai, a haka wata rana Alghabit ya sake komawa fatauci, a lokacin ne Suley ya fahimci wani ha'inci da ake mishi idan baya nan kuma a cikin gidanshi, babbar 'yarsa *Zeeya'atu* wacce gaba d'aya shekarunta basu haura sha shida ba tana ganin ya bar garin ita ma zata fara na ta yawon dan jin dad'in rayuwarta, kuma mahaifiyarta *Zaha* iya ke d'aure mata gindi tana bata umarni, babban tashin hankalin shine wani lokaci har ta kan iya kwana ba gida ba, nan yayi niyyar sanar da mai gidan idan ya dawo, domin kuwa babu mai zarginta, dan idan ta tashi fitar ta kanyi shiga ta kammala sannan tayi nesa da gida. Bayan Alghabit ya dawo tuni sauran yaran dake tayashi kasuwanci suka rigashi isowa tare da sauran rak'uman dake d'auke da kaya, dan haka kai tsaye ya wuce kasuwar garin dan a sauke wannan kayan a rabawa k'ananan yan kasuwa, a nan fa yayi kicib'us da Suley a cikin masu sauke kayan, wannan abu shi ya birgeshi a tare da yaron ya kuma ji ya yarda dashi ba ko kokonto, hakanne yasa ko da suka iso gida bai bawa Suley damar fad'in abinda yayi niyyar fad'a ba yace ya d'ora shi akan harkokinshi, yanzu ya zama kamar magajinshi zai dinga tafiyar da komai, wannan karamcin da wa suley ya sa bai iya fad'an komai ba saboda kunya, ba b'ata lokaci Suley ya durmiya cikin kasuwanci ya fara sarrafa dukiyar yanda ya kamata, sai Allah yayi wa Suley baiwa ta nasibi ta yanda duk abinda ya tab'a yakan hauhawa, cikin wata *uku* sai gashi shi kanshi alghabit na mamakin yanda dukiyar take bunk'asa, sai kawai ya sake yarda da shi ta yanda wata ranar *alhamis* ya shirya yace wa mutanen gidan zaiyi wata yar gajeriyar tafiya ya dawo, fatan alkairi suka mishi amma babu wanda tunaninshi ya bashi wani abu. Sam Suley baya dawowa idan ya fita sai yamma, amma a ranar mantuwar da yayi tasa shi dawowa gidan lokacin da bai kamata, bai samu kowa a tsakar gidan ba dan haka ya shiga d'akin shi dake farkon shiga gidan, ya d'auko sak'on ya fito ya rufe d'aki zai juya kenan yaji sauti kamar kukan Zeeya'atu, A hankali ya dawo ya d'an daga k'afafun shi ya lek'o ta katangar data mishi shamaki da nasu d'akunan, ashe ciki ne da ita mahaifiyarta kuma ta amso mata maganin gargajiya dan cikin ya zube, ganin jini duk ya b'ata mata jiki ga bala'in kukan da take uwar na k'ok'arin shigar da ita d'aki yasa shi sukwanowa da nufin taimaka musu, yana daf da isa wurin su basu san da shi ba mahaifiyarta tace a harshen buzanci "Dangana mana Zeeya, ke da kin samu ma cikin zai zube." Duk da bai iya komai a hausarsu ba amma yana jin d'aid'ai, a cikin hakane ma ya gane ta ambaci sunan ciki, da kuma zubewa amma sauran kam baiji komai ba sai dai kasancewar shi matashi mai matuk'ar basira da d'aukar duk abinda yaji yasa ya hardace kalaman data fad'a a buzancin, juyowa yayi ya fita ya barsu nan, yaje kasuwa ya kai sak'on yana cin abincinshi na rana tare da wani shi ma yaron Alghabit ne, da k'yar yaron ya fahimci abinda suley ya fad'a mishi yace yana son sanin fassarar , haka dai ya had'a haussar da k'yar ya fad'a mishi abinda ake nufi, sosai wannan al'amari ya girgiza shi ya kuma yi niyyar fad'awa mai gidanshi. *K'addara ta riga fata* Ko da ya samu alghabit dan sanar dashi sai ya katseshi tare da cewa ya kira mishi liman, bayan sun dawo tare da liman ya kira Zaha da Zeeya, bud'ar bakin Alghabit shine ya baiwa Suley 'yarshi Zeeya'atu wacce yafi so da k'auna, kuma baya buk'atar komai daga gare shi sadaki ma shine zai biya a matsayinshi na uban Suley, da sauri Suley ya kalleshi gabanshi na tsananta bugawa, juyawa yayi a hankali ya kalli Zeeya wacce take jin kamar ta mutu tsabar bak'in ciki, amma son nuna ita saliha ce yasa ko d'agowa ba tayi ba, zaha kuma kuma ba tace bata ji dad'i ba ba tace taji dad'i ba, kowa da abinda yake tunanin a zuciyarshi har Alghabit ya katsesu da cewa zai basu gidan da zasu zauna kuma gidan ya mallakawa Suley halak malak, sannan ya k'ara da cewa ya ware mishi jari mai yawa da zai tsaya da k'afar shi shima, wannan abun ne yasa Suley yin shiru ya karb'i auren Zeeya, gashi kuma Alghabit yace za'a d'aura auren juma'a ne ba b'ata lokaci. *Allah ka gafarta mana.* 10/06/2020 à 12:07 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _13_ Lafiya lau Suley ya zo maradi kuma wannan karan tafiyar tashi tayi goshi, domin kuwa da idonshi yaga k'anwar shi da irin mummunar rayuwar da take, wacce a lokacin take d'auke da yaronta Labaran daya ke da shekara d'aya da haihuwa, wani ikon ubangiji cikin sauk'i Suley ya shawo kanta suka dawo gida tare, amma bata yarda ta biyo shi gidan mahaifinsu ba saida ya tabbatar mata da yana da kud'i zai siye musu gida su zauna tare saiya kawo iyalinshi, kasancewar lokacin akwai albarkar rayuwa yasa ya siye lafiyayyen gida kuma a farashi mai sauk'i, gyara yasa aka ma gidan sosai tare da ware d'akuna uku, nashi, na Zeeya, na Husseina, saida aka gama gyaran gidan Husseina ta tare a ciki sannan ya juya ya koma agadez dan sanar da mutanen can halin da ake ciki tunda ba waya ke akwai ba a lokacin, nan Husseina ta ci gaba da zama a gidan tana jiran dawowarshi, babu wani abu da bai bar mata ba duk dan tsoron karta sake sub'uce musu, wanda wannan zaman da tayi kuma mutane aka sake d'ora mata ido, dan dama gidan daya siye ba nesa ne sosai da gidan nasu ba wanda yanzu daga Ramma sai Innusa a gidan da matanshi biyu, haka yaje gida lfy kuma tun a zuwanshi iyalinshi Zeeya ya fara yi wa magana akan komai, kuskuren da yayi shine sanar da ita da yayi halin da Husseina ke ciki tunda farkon abinda ya faru har k'arshe, sannan yace a matsayinshi n'a mijinta dole ta shirya su koma mahaifarshi tare. Kamar dai yanda yasan zai faru hakane kuwa, domin direwa tayi tace Allah ya tsareta da komawa garinshi ta bar na ta garin, kwana hud'u ya d'auka yana lallab'ata kan ta shirya su tafi amma tana botsarewa, dan haka k'arshe ya samu iyayenta ya fad'a musu komai da ake ciki, Allah sarki dattijon arziki Alghabit, nan ya rufe ido duk da son da yake mata ya mata tatas tare da bata umarnin ta had'a kayanta su tafi, sannan yace Suley zai iya siyar da gidan daya bashi saiya k'ara ya ci gaba da kasuwancinshi, haka kuwa akayi sai dai hakan ya d'auke shi kusan wata d'aya kafin suka d'auko hanya kuma suka zo da izinin ubangiji. Duk da a lokacin ana ganin yara 'yan biyu, amma ganin 'yan uku kam ba'a cika samu ba, dan haka wannan yara na Suley sai suka samu farin jini a cikin unguwarsu fiye da kima, gasu kuma dama sak mahaifiyarsu suka d'auka buzuwa jawur da su kuma tub'ur tub'ur, hakan yasa mutanen sintiri cikin gidan ana duba yaran wasu ma har uwar kallonta suke suna son tayi magana suji harshenta da hausarta ke da ban sha'awa da dariya, sai dai ba anan gizo yake sak'ar ba, tunda suka zo ta ga d'akin daya fitar ma da Husseina ma had'e yake da nata saita mayar da ita kamar kishiyarta, wani haushinta take ji tare da k'yamarta, ita ma Husseina a lokacin da sauran d'anyan kai na rayuwar da tayi saiya zama babu ruwanta da harkar matar yayan nata, dan haka babu mai shiga shirgin kowa, hatta yaranta Zeeya bata bari ko da rarrafe suje d'akin ta, suna dosa zata taro su tana habaici da bak'ak'en maganganu a harshenta na buzanci, Husseina kuma tunda ta fahimci yayanta ma zaman hak'uri yake da ita kuma kullum yana cewa tayi hak'uri da halin Zeeya'atu sai kawai take ba banza ajiyarta, duk da zamansu gida d'aya baisa ta d'aga mishi k'afa ba na salon rashin mutumci, zai kawo abinci mai rai da lafiya ta sarrafa amma idan ta gama sai tace bata dafa da shi ba sai ita sai 'ya'yanta, shi kuma sai yace yaji dad'i tunda ma an dafa da 'ya'yan nashi, maganar saduwa kam shi har ma ya manta rabon daya kusanceta, dan tun kafin su fahimci tana da ciki, yanzu kuma daya nuna mata buk'atar shi sai tace ai ina, bata sake shirya haihuwar wasu yaran ba, idan ya isheta da magiya saita dinga cewa wai ai da karuwa a gidan yaje ya biya kud'in shi mana ya samu nutsuwa, hakan yana k'ona masa rai sosai, da wannan rayuwa har ya saba da shan jar kanwa da lemun tsami, Husseina kuma ta fad'awa yer uwarta Hassana wacce ke gidan aurenta ita ma halin da d'an uwansu ke ciki, shawartarshi sukayi yayi aure, kuma bai watsa musu k'asa a ido ba, sai dai Allah ya hukunta Zeeya ita ce matarshi ta har abada a duniya, watak'ila tanadin da ubangiji ya mishi ne mai girma a lahira, shiyasa duk yarinyar daya nema maganar bata zuwa ko ina sai a barta, harya gaji yace ya hak'ura ba zai zama kamar mane-min mata ba kullum a hanyar zuwa gidan yan mata, mutane kuma da 'yan uwa sun alak'anta hakan da Zeeya wacce take kallonsu tace eh tabbas ita ce, ba zai tab'a had'a ta da wata mata a duniya ba, kuma har ga Allah babu boka babu malam a lamarinta, kawai tana tauna tsakuwa ne dan aya taji tsoro, k'iyayyar Husseina ta sake hudawa ta shiga zuciyar Zeeya a sanda duk in ta k'i bashi abinci ita take bashi, ya zamana ma harda rana ita ke dafawa tana zuwa kasuwa da kanta tana kai mishi, hakan yasa take ganin ba tada maraba da kishiyarta, saidai duk masifar da take daga Suley har Husseina babu mai tanka mata. Shekaru na ja duniya ana sake ci gaba zamani na k'ara shigowa, kai ya waye ta yanda kowane yaro akan saka shi makaranta dan yak'ar jahilci, sai dai ga wanda kan nasa bai waye ba kawai, a lokacin ana shiga ajin farko da shekara bakwai, haka Suley ya had'a duka yaran harda Labaran ma daya d'an fisu da watanni aka kaisu makaranta aka saka, takaici kamar zai kasheta dan bata so hakan ba, shiyasa har yaran saida suka shiga uku, dan dukansu take sosai tana cewa babu su babu d'an karuwar nan, amma abinka ga yaro yanzu yanzu ne zata sake ganin sun had'e wuri d'aya, musamman ma Hussein da yafi sauran zuciya, tana dukanshi zai koma bakin k'ofa yace anje anyi, shi kuma Labaran yaran sun shiga ranshi sosai, suna matuk'ar birgeshi sosai sosai, yana mamakin ganinsu su uku duk iri d'aya, haka zai saka su gaba ya tab'a hancin wannan ya duba yatsunsu ya ga kala d'aya, yace suyi dariya ya ga iri d'aya wannan yasa yake k'aunarsu sosai, haka suke zuwa makarantarsu tare suna dawowa, wani hukunci na Allah kuma sai Labaran ya zab'i zama kamar Suley ma'ana d'an kasuwa, cewa yake shi zai dinga binshi kasuwa ya daina zuwa makaranta, amma Suley yace yaje yayi karatu da hakane zai zama d'an kasuwa mai ilimi ba jahili ba, Hassan shima da abinda yake son zama, domin yaro ne mai son k'irk'irar abu da kanshi, haka ma Hussein yana son ya ga ya zama matuk'in jirgin sama wanda a lokacin idan ya wuce zakaga har babba ma ya d'aga kai sama ya kalla, Gambo kuma tunda ya samu Suley wata rana yana shan lemun tsami ya tambaya shi dalili yace cikinshi kawai ke ciwo, sai ya d'auri niyyar zama babban likita danya warkar da mahaifinshi, amma sakamakon wani abu daya shigo ya gifta ya musu shamaki da cikar burinsu wanda zasu iya kiranshi da k'addararsu sai kowa ya zama abinda bashi yake so ya zama ba, hakan kuma ya faru ne sanadiyar jiji da kan uwarsu da kuma son cika nata burin. Innusa yayan Suley ne ya kwanta rashin lafiya mai tsanani, Suley na shiga gidan ya ganshi sai dai baya samun wani sakin fuska daga kan Ramma har shi Innusa, domin kuwa suna matuk'ar jin zafin ci gaban da yake samu a harkokinshi, dan Suley mutum ne mai k'wazo, duk abinda yasan zai samu riba a kai to ya kan siyoshi ya siyar, ya zama d'an kasuwa da ake ji da shi a wannan lokacin, sannan matarshi da suke gani buzuwa ce wanda a lokacin sun san auren buzuwa *jidali* ne kamar yanda wani mawak'i ya fad'a, har yan uku yaje dasu sun ga baffan nasu har Gambo yana cewa idan ya zama likita zai bashi magani ya warke, Zeeya ce bata je ba dan haka Suley yace taje ta dubashi, kunsan dai halin kayan gidan Suley sai kuwa tace babu inda zata je, wannan karan bud'e mata ido yayi yace wallahi ko a kai ne saiya d'auketa, hakan ne yasa ta shiryawa suka tafi tare da dare, wata atamfa ce a jikinta wacce a wannan zamani sai wane da wane mai sunan *ABC* a jikinta, hak'ik'a tasan mijinta namiji ne na gaske, dan duk abinda zai shigo dashi garin nan komai tsadarshi saiya fara kawo mata shi kafin ya fara siyarwa a gari, d'inkin riga da zane ne aka mata wacce rigar aka mata tattara da robo take ja sosai, kallabin daya kamata ta d'aura shi ta d'aura a k'ugu (wanda kowa yasan a zamanin iyayenmu da kakaninmu wannan ba wani abu bane dan mace ta fita kai sake, musamman idan aka ce ma anyiwa kan gyara), dama kuma ba kasafai aka cika saka gyale ba, sai dai a yafa zanin atamfar a mazaunin gyalen, maimakon ta d'ora zanin ta rufe kanta sai kawai ta ninkeshi gida biyu ta d'ora saman kafad'a, takalminta ta saka bak'ak'e k'afa ciki masu tudu sosai, inda kuma kanta ya ci uban gyara (coiffure) sai k'amshi yake da walk'iya, a haka fa suka jero suka zo har gidan duk da babu nisa, tunda suka shigo matan gidan da yara ke kallonta, hak'ik'a fa ta had'u sosai, sai dai bak'in ciki kawai da hassada ya hanaka fad'an hakan, Suley kawai ke gaisawa da su suna amsawa sama sama yana tambayar mai jiki, saida ya gama tsaf kafin Zeeya ta kalli Ramma cikin ido tace "Ya mai jikin?" Ita ma kamar yanda ta tambaya haka ta mayar mata da "Mai jiki da sauk'i." K'ala ba tace ba dan ita ma ba k'aunar su take ba kamar yanda basa k'aunar ta da kuma mijinta da yaranta, tun a labarin daya bata da kuma yanda yanzu suke zaune anan shekara kusan tara kenan ta fahimci haka, ita kuma duk wanda baya k'aunar mijinta da zuri'arta ita ce baya so, dan ita fa tana mugun bala'in son Suley, kawai dai tuna yanda aurensu ya kasance ne da irin zaman da sukayi yasa take jin ba zata iya neman sulhu ba ko ta kyautata mishi, mik'ewa sukayi zasu tafi tana gaba Suley ya ciro kud'i masu yawa ya aje gaban shinfid'ar Innusa yace a siya mishi magani, kullum idan ya zo ya bayar suna karb'a, amma yau Innusa daya kalli matar Suley ya ga ta take nashi matan har biyu, ga uban shirin da tayi sai ranshi ya b'ace, d'aukar kud'in yayi ya watso mishi yana fad'in "D'auki tsiyarka bana so, da can kai kake siya min maganin, ni zaka wa birgar mata, to bana son alfarmarka, dan wannan kud'in ganinsu nake kamar alfarma ce daga gareka, ni kuma duk wata alfarma da zata fito daga wajenka bana buk'atar ta a gidan duniyar nan, Suley babu ni babu kai wallahi na tsaneka." Zeeya da tunda ya fara magana ta dawo ta tsaya take kallonshi , kallon Suley tayi taga sai doka murmushi take yana girgiza kai, a hankali yace "Allah ya baka lafiya kai dai, nasan zafin ciwo ne." Haushi ne yasa taji kamar ta mare shi, dan haka ita ta kalli Innusa tace "Ka ce baka son alfarma kowace iri ce indai daga *Suleyy* ta fito?" Kallonta Suley yayi saboda wani bala'in dad'i da yaji sunanshi yayi a bakinta, bai tab'a jin sunan cikin nutsuwa ba kamar yau, Innusa ne yace "Eh haka nace, ke ba tashi ma kaf zuri'ar shi da zuri'ata ba ma buk'ata, kuma ko bayan raina ban lamunce wani daga cikin tsatsona ya nemi alfarma ko taimakon zuri'ar Suley ba." Murmushi tayi tace "Ni kuma Zeeya'atu muddin ina numfashi a doran k'asa sai na saka neman alfarmar Suley, idan haka bata faru ba to ka sani zuri'ar ka zata nemi taimakon zuri'ar Suley da ikon Allah, ka rubuta wannan ka aje ka kuma d'auka yanzu fad'an tsakani na da kai ne ba da mijina ba, dan shi yafi k'arfin ajinka yanzu." Tana fad'a ta juya ta kama hannun Suley kamar yaro suka fita, kallonta kawai yake yana mamakinta, shin abinda aka mishi ne ya b'ata mata rai? To meyasa? Saboda tana sona? To meyasa bata nuna min soyayyar? Da haka suka k'arasa gida har ciki d'aki kafin ta saki hannunshi, ganin kallon da yake mata yasa ta fara cire shirin jikinta dan ta rage ma kanta nauyi, Suley na ganin haka saiya durmiya da ita duniyar maji dad'i daya jima har ya manta rabon da yaje can d'in, ita kanta fa ta gane tayi kewarshi sosai, *wannan rana*, *wannan dare*, shine ya shiga cikin tarihin rayuwar aurensu da ba zasu tab'a mantawa ba, kwana sukayi suna fad'awa juna kalamai masu taushi, kwana sukayi suna gajiyar da junansu da nuna yanda sukayi kewar juna, yan uku ma sai d'akin Husseina suka kwana da sukaji iyayen na su sun k'i bud'e musu k'ofa. *Abu* kamar ya canza ashe ba haka bane, dan tunda gari ya waye Suley ya fahimci hakan, har yanzu dai ba wata girmamawa tsakaninsu, sai dai duk wannan billin rashin mutumcin da d'aga mishi murya ta daina, abinci ma yanzu har na safiya kawo mishi take ko ta aika cikin yaran wani ya kai mishi, idan an kwana biyu kuma ta kan ziyarce shi har d'akin shi ya d'an samu nutsuwa, kuma duk da haka tana nan tana tunanin hanyar da zata saka Innusa neman alfarma ko taimako wata rana, tana ji a jikinta zamani zai zo da komai zai zama ko dai d'an kud'i ko kuma alfarma, da wannan harta samu tsayayyar magana ta kuma tsaya a kanta. A cikin shekaru *goma sha biyu* Zeeya bata sake haihuwa ba sai b'ari data dinga yi har sau biyar, hakan yasa tace ma Suley ta hak'ura da haihuwar kawai Allah ya raya mata ukun ma, tuni kuma lokacin ta juya akalar burin kowa izuwa nata burin, tun farko data nuna ga aikin da take su suyi basuyi mata musu ba, dan dama ita ce mala'ikan gidan mai horo, dan Abbansu babu ruwanshi tsakaninsu dashi wasa da dariya ne, amma ita babu wannan sai had'e fuska kamar sojiya,😂 Hassan ya duk'ufa nashi karatun inda yana kammalawa kafin ya samu aiki tace ai dole yayi aure, har Suley yace mata da son samu ne a aurar dasu baki d'aya, amma gudun kar ya kawo mata zab'inshi wacce zata zo ta sauya mata ra'ayin yara daga yanda suke mata biyayya yasa ta k'i yarda, haka yaran suka nunawa mahaifinshi ya rabu da ita kawai zasu mata biyayya, kuma kullum dama idan ya so mata magana akan tsaurin da take musu su ke nuna babu komai, saiya zab'i yayi shiru dan kar yaran su fahimci akwai rashin jituwa tsakaninsu da har zai saka su dinga saka bakinsu a al'amarinsu, *Sa'ada* yar aminiyarta ce wacce ke Agadez ita ma, sanin babu ruwanta ita da yarinyar tana musu kallon kidahumai yasa ta nema mishi aurenta, duk ba'a b'ata lokaci ba akayi komai aka gama, kasancewar tana karatu yasa bayan auren aka nema mata gurbin karatu anan ta ci gaba, duk da babu soyayya tsakaninsu suna mutumta junansu da girmamawa, baifi wata d'aya da aurensu ba Allah ya bata cikin ' yan biyu, lokacin kuma Hussein ya dawo gida hutu shima aka fara maganar aure, sai dai tace bata ga yarinyar data dace da Hussein ba, tana buk'atar yarinya wacce bata da wayewa da zurfin ilimi ta yanda ba zata damu ko saka ma rayuwar d'an ta ido ba, sannan wacce bata da wani gata ta yanda ko ya daketa zai daki banza (😂) dan ta sanshi da zuciya, yana da kwana biyar da zuwa ya tuk'a Hajia da kanshi ya kaita bikin 'yar k'awarta a Zinder, to fa anan ta had'u da *Zeinabu* a cikin k'awayen amarya take, duk yanda ta so ta kasance haka take, bugu da k'ari iyayenta sun rasu tana hannun kakarta ne *Inna* wacce ta haifi Babanta, su ma dai ba'a d'auki lokaci ba aka fara shirye shirye, su suna ganin zasu shiga babban gida ne, dan wannan lokacin *Alhaji Suleymane Hassan Gaga* ya zama d'an kasuwa lamba d'aya wanda ya zama komai da ruwanka, kampanin buga ledoji, kampanin sarrafa pliwa da sukari, kampanin sarrafa duk wani abu daya shafi roba irinsu robobi, bokiti tabarma da takalma na roba, gidajen mai wanda lokacin basuyi yawa sosai ba, baya ga shaguna ba adadi, da kuma kampaninshi na buga atamfofin dake garin *Niamey* , ya dai zama kicima shima, dan haka suke cewa kakarsu ya yanke sak'a, *(kuna musu kallon biri suna muku kallon bishiyar hawa)*, lokacin da aka saka ne ya bawa Hussein damar yin tafiya kafin lokacin, duka wata biyu yayi sai suka zo Zinder za ayi *18 Décembre* anan, bayan an kammala ana ta shirye shiryen komawa Hajia tace dole ya kira Zeinabu yaje ya sameta su gaisa karya yarda ya bar garin nan basu ga juna ba, Hussein ya kira Zeinabu da yar wayarta yace ta zo su gaisa kafin ya wuce dan shi ko gidansu bai sani ba saita waya dama suke gaisawa, Inna da rawar k'afa ita ta tayata shiryawa aka fesa mata turaruka sannan ta tafi a taxi, haka taje compagnie wajenshi babu mai tunanin faruwar wani abu a cikinsu, turarukan data fesa yasa hankalin Hussein tashi, hakan ya ingizashi har yayi abinda bai tab'a yi ba, duk da yaga Zeinabu kuma bata wani birgeshi ba, amma hakan ya kawar da budurcinta a wannan ranar, duk da ta so bijire masa amma daya tuna mata shine zai aureta sai tayi shiru ita ma, a wannan tarraya ne aka samu cikin *Junaid*. Ana gobe d'aurin aure Inna taga laulayin Zeinabu yayi yawa, tana dubata ta gane ciki ne da ita, ko da ta tambayeta wane shegen ne? Ta fad'a mata wanda zata aura saida ta sauke ajiyar zuciya, nan tasa ta kirashi a waya wai yazo, ba tare da shakku ba yace idan ya zo me zai mata? Inna dai da taga yaron fitananne ne ba zai zo ba sai kawai ta amshi wayar ta fad'a mishi komai tare da cewa ita zata sanar ma da iyayenshi, nan fa hankalinshi ya tashi dan ba zai ce k'arya bane, sulhu ya nema anan ne fa Inna tace zata rufa asiri amma dole ya biyata, nan tace tunda dama ba mataimaki gareta ba to ya d'auke mata abinci da sutura, ba musu ya amince da hakan inda washe gari aka d'aura aure sukayi gum da bakinsu. Bayan aurensu da wata uku Sa'ada ta haihu kuma 'yan biyu, *Ammar* da *Amar*, Hajia na d'ora ido a kansu Amar ne yafi shiga ranta, tana kallonshi kawai taji kamar yaranta ne take kallo lokacin data haihu, Ammar kuma daya cika asibitin da kuka sai take ta mishi sharri wanda mutane ke dariya ana ganin na kaka da jika ne, to fa da irin wannan hantarar ta gina rashin jituwa tsakaninta da Ammar, iyayensu ma da suka gane tafi k'aunar Amar sai suka fi mayar da hankalinsu kanshi, indai suna gabanta duk abinda Ammar zaiyi sai sun hantareshi da zaginshi dan jin dad'in ta, Amar kuma baya laifi a wajensu dan ko bata gidan babu mai dukanshi, dan tsaf zata gurza maka rashin mutumci ko uban daya haife shi ne, a wannan lokacin cikin Zeinabu na wata hud'u, Husseina ma sai tace Labaran yayi aure dan tunda yasan ta hanyar da aka haifeshi ya mayar da hankalinshi kan kasuwanci harya tsaya da kafarshi, da k'yar ya samu yarinya mai nutsuwa da hankali wato *Soueiba*, amma data amince tana son shi tsaf ya fad'a mata tarihinshi bayan ta mishi alk'awarin ba zata gujeshi ba, haka tace taji ta gani kuma daga shi har mahaifiyarshi babu mai laifi, girma da mutumcin Suley da ake gani a gari yasa iyayenta basu wani zurfafa bincike ba suka bashi aurenta, dan dayawa d'auka suke Husseina matar Suley ce saboda har wannan lokacin miji bai samu ba, suma anyi aure lafiya lau lokacin kuma aka haifi Junaid, kuma suna da wata tara da aure ta haihu, bayan watanni ma Soueiba ta haifi Jibril. *Bayan shekaru biyar* Gambo data durmiyashi cikin siyasa ya samu nutsuwa, yana zuwa tace mishi ta mishi mata aure zaiyi, bai ja da maganar ba shima ya amince, *Hadiza*, ita ce yarinyar data zab'a mishi wacce anan unguwarsu take, sam Hadiza bata son shi dan tana da wanda take so, amma fin k'arfi da ganin matsayinshi yasa babu yanda ta iya, had'a kai 'yan uku sukayi suka had'a k'arfi da k'arfe suka gwangwaza sabon gini na gani na fad'a a wannan zamani, a *ADS* suka buga wannan gini tun lokacin unguwar babu mutane dayawa sai wane da wane, haka akayi tsari mai kyau a lokacin aka d'aura auren Gambo, tare suka dawo gidan dukansu harda su Labaran da suke jin ba zasu iya rayuwa da su ba dan sun zama d'aya, Zeeya tayi farin ciki da hura hanci da k'afafa ganin gidan da yaranta suka gina, sai dai bata ji dad'in tarewarsu tare da su Husseina ba sai taga kamar sun zamar mata k'arfen k'afa. *I ❤ u true fan's* 10/06/2020 à 12:07 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _14_ Tunda Hadiza ta tare gidan ta fahimci sauran matan da ma mutanen gidan baki d'aya hak'uri suke da tsohuwar gidan, ita kuma sai take ganin ba zata iya ba gaskiya, domin kuwa ba zatayi hak'uri da tilasta mata da akayi ba ta auri d'an ta, sannan kuma tayi hak'uri da rashin mutumcin da uwarshi ke darzawa a gidan, duk da bata nuna mishi k'iyayya a zahiri amma dai da gani kasan ba wai dan tana so bane take zaune da shi, dan ko mu'amuma ta aure ya nemeta zakaga tana irin gani kayi yanda zakayi kawai na kama gabana take mishi, haka zaka ga tana wani kakkawar da kai tana gunguni da k'ananun tsaki da baya fitowa fili, ya jima da fahimtar hakan, shi kuma Allah ya san zuciyarshi baisan lokacin data shiga ta shi zuciyar ba, dan haka yake k'ok'ari sosai wajen faranta mata rai duk da bai cika zama tare da su ba, kulawar da yake nuna mata da kaffa-kaffa da rashin son b'acin ranta yasa Hajia lura da hakan, nan ita ma saita fara kafa mata k'ahon zuk'a ta hanyar nuna mata tsana a fili da cewa bata isa ta rabata da d'an ta ba ko da me ta shigo, sam bata kula ta saboda ko ba komai babba ce ita kuma ta haifi mijinta, sai dai ita kuma bata cika yin irin bautar da take saka Zeinabu da Soueiba ba da Sa'ada, ko sun fara aikin tare zata zame ta kawo na ta fi'ilin, a lokacin Sa'ada ita ma hak'uri take sosai, badan ma karatun ta data saka gaba ba wanda Hajiar ta so datseshi, amma da k'yar Hassan ya fad'awa Suley daya fahimci tana son karatun sannan suka shawo kan matsalar, duk da jimawar da tayi bata samu ciki ba hakan bai damu Hajia ba, dan ita a ganinta ma hakan daidai ne, dan yanda ita kad'ai ma ta mallake mata d'a ina ga ta haihu, saidai bata d'aga musu k'afa har zuwa lokacin, duk wata hidima ta gidan sune har da hidimar ita kanta, idan ka same su da rana zaka rantse masu aiki ne ba matan gidan ba, gashi kuma a lokacin Allah yasa duk mazajen nasu babu wanda bai samu k'arin matsayi ba, amma haka suke rayuwar k'ask'anci kamar bayi, ko fita zasuyi sai Hajia ta bada izini, dan haka tun kana jibi zaka fita kake sanar da ita dan ta baka lokacin data ke so, girman ciki ko tsufanshi baya sa ta sarara maka da aikin gida, saika haihu kawai kake da damar yin jego na sati d'aya shima saboda idon mutane, wani ikon Allah kuma har saida Hadiza ta shekara *shida* a gidan kafin Allah ya bata cikin su Hamna, ciki ne daya bata wahala sosai, hakan yasa fa Gambo ya rufe ido ya shirya sai kawai Hajia ganinshi tayi da kaya yace zai tafi da matarshi can ya samu k'wararrin likitoci da zasu dinga dubata, a lokacin Hajia bata iya cewa komai ba saboda Suley dake wurin kuma yace ba komai su tafi Allah ya tsare, daga lokacin ta sa k'afar wando d'aya da su dukansu, ko kiranta sukayi a waya dan su gaisheta sai dai ta kashe kiran, sam ta fita a lamarinsu ta zura musu ido, shi kuma yana can duk da yana damuwa sosai da hushin da Hajiar keyi amma baya hana shi kulawa da ita, sosai yake nuna mata soyayya, amma zuciyarta kamar ta shed'an sam ta k'i saduda ta so shi daidai da k'wayar zarra, suna haka har ta haihu ta samu *Hamna* da *Amna*, yara ne da za ace basuyi goshi ba a wajen Hajia, dan da suka dawo ma dan ayi suna anan ko kallon yaran batayi ba, hakan baya musu dad'i amma ya zasuyi daya wuce rarrashi harta yafe musu, abu ya k'i ci ya k'i cinyewa, sai Hadiza tayi anfani da wannan dama ta hanyar nuna mishi gwara ya rabu da ita danya shirya da mahaifiyarshi, tambayar daya jefa mata a lokacin tasa t saurin kallonshi, domin kuwa cewa yayi "Har yanzu na kasa samun shiga zuciyarki ko?" Kame kame kawai ta dinga yi masa har yace ta fad'a mishi gaskiya tsakaninta da Allah tana son zama da shi ko bata so, ganin ba zata iya tauye kanta ba yasa ta fad'a mishi gaskiya hak'uri take amma bata sonshi har yanzu, duk da hakan bai mishi dad'i ba amma ba zai iya tauyeta ba, dan inhar zai kasa samun zuciyarta a shekara shida duk da kyautata mata da yake, to fa baiga ranar da zata so shi ba, a wannan lokaci ne ya saketa saki d'aya yace zata iya aure idan ta samu miji, su Hamna kuma da ko arba'in d'in su ba ayi ba yace ta shayar dasu idan ta yayesu zai d'auko yaranshi, gaba d'aya kuma sai hakan bai mata dad'i ba taji jikinta yayi sanyi, amma aikin gama ya riga daya gama kuma, jin wannan labari yasa Hajia shiryawa da shi, rufe ido tayi tace ai dole sai dai ta bar su Hamna ita ta tafi saboda ta nuna mata basa buk'atar ta suma tunda ta nuna bata buk'atar su, irin tarzomar da akayi ba k'arama bace akan yaran, dan ita ma Hadiza zuciya tayi ta aje yaran tace gasu nan ta shayar dasu idan zata iya, Suley kuma da Gambo suna rarrashinta amma ido sun rufe, haka ta fita a gidan daga ita sai kayan da aka kawota da su, tace yara Allah ya raya mata su idan sun girma zasu nemeta, Hajia kuma tace ba zata hana su nemeta ba amma dai ba zata tab'a cin moriyarsu ba, bayan ta barsu da fari Sa'ada tace wai dole ta sha maganin da zai dawo mata da ruwan nono dan lokacin ita ma shiru tun su Ammar saboda ta shayar dasu Hamna, Alhaji ne yace ba zai tab'a faruwa ba, idan kuma yaran suka tasa suka zo junansu fa, kuma ko ba komai ma zasu iya had'a su auren zumunci, dan haka sai dai tasan yanda zatayi da yaran, dan ta nuna musu a shirye take yasa ta samu madara aka dinga basu, amma rainon yaran kuma Sa'ada ce keyi wacce ke karatun likitar ta a lokacin, a haka su Hamna ke wayo suna girma har Sa'ada ta so tafiya France dan zama doctorat, amma Hajia tace ina ba'a gidan nan ba, wanda tayi ma babu yanda zatayi ne, haka ta hak'ura ta barwa Allah, wanda lokacin ne kuma Hajia tace dole sai dai Junaid ya zama malamin makaranta, Amar kuma cikin ruwan sanyi ake ce shalele ya zama ma'aikacin banki, Ammar kuma da kullum suna tare da kawunshi indai yana gari babu abinda yake so daya wuce ya sa hular soja ya daidaita mata zama, sai Hajia tace ya zama likita shi yafi mishi, bore yayi yace sam sai dai ya nemi kud'i ya kai kanshi inda zai zama abinda yake so, amma haka Sa'ada ta rarrasheshi tace ya cika mata burinta sai su zama likitoci suna zuwa aiki tare, badan wannan dubara ba da fa sai dai idan sunji k'arar bindiga su fito suga Ammar ne ya zama soja, gashi Innusa da yasa ta d'auki wannan alhwashin ma ko kula da tsiyarsu bayayi, har yanzu jituwa ta kasa shiga tsakaninsu, su Ramma an jima da barin duniya, amma shi da yan uwanshi sun k'i d'aukar Suley a matsayin d'an uwa, komai zasuyi su kan wareshi ne, lokuta da dama idan zasu aurar da d'aya daga cikin yayansu sai dai yaji a gari, amma hakan baya hanashi fad'awa iyalinshi kuma ya umarcesu da su tafi, amma banda Zeeya wacce baya ma fara cewa ta tafi d'in, sai dai bamu sani ba ko anan gaba zasu iya neman alfarmar ko taimako, domin kuwa a cikin zuri'ar Innusa akwai d'alibai da dama masu neman ilimi, sannan akwai 'yan kasuwa, masu shigowa da kaya, haka kuma 'yan kwangila da wani lokacin kud'in da aka basu suke musu k'aranci dole sukan nemi bashi a hannun banki, sannan shi kanshi Innusa yana fama da ciwon k'afar da har ya fara shafar zuciyarshi. *CI GABAN LABARI* Koda suka shiga b'angaren su kowa d'akin shi ya nufa ya shiga wanka, sai dai babu mai kuzari a tare da shi har suka fara fitowa, Junaid ne ya tarar da Jibril zaune ya k'urawa tv ido, zaune yayi shima ya kalleshi yace "Jibril tunanin Amna kake ko? Kayi hak'uri kaji, watak'ila hakan shiya fi zama alkairi a wajenka, muyi addu'a kawai Allah ya bamu hak'uri da juriyar cin wannan jarabawa." Numfashi ya sauke mai k'arfi ya kalleshi da murmushi yace "Sam d'an uwa ba abinda nake tunani ba kenan, yau ina cikin farin ciki Junaid, ni da ban tab'a ganin soyayya daga wurin Hajia ba, yau sai gashi ta kalleni tace ta bani Jamila, wacce daga tsatsonta ta fito, gaskiya naji dad'in haka, duk da ban samu Amna ba amma nayi farin ciki sosai da hakan." Amar daya shirya zai fito ne yaji suna hira dan haka ya tsaya yana saurare, Junaid ne yace "Ni ma ban k'i Hamna ba, amma ka tayani tunani mana, yanzu me iyayen Maryama zasuyi tunani? Zasu d'auke ni mak'aryaci kenan d'an k'ananan mutane? Sannan ita idan ta jini shiru za tace na gudu kenan ko kuma dama mayaudari ne ni? Wannan abun nake ta tunani wallahi." Cike da nuna damuwa Jibril yace "To meye abunyi yanzu? Gaskiya bai kamata ace ka bar Maryama a wannan rayuwar ba, ko da alk'awarin daka d'auka na zaka mayar da ita gida ne ka cika, sauran saika musu bayani yanda zasu fahimta." Jingina bayanshi yayi a kujera yace "Da ace zata lamunce min wallahi dana had'a na auri mata biyu a lokaci d'aya, sai dai nasan ba lallai ta amince ba." Ammar ne ya bud'o k'ofa ya fito hakan yasa Amar k'arasa fitowa shima, abun mamaki kayan baccin jikinsu iri d'aya ne, dan dama sau tari sukan samu wannan kamanceceniyar, kallon juna sukayi wanda yasa Ammar yin tsaki yace "Je ka cire kayan nan." Amar da baya yanayin farin ciki yace "Saboda me? Idan ka damu kai ka cire naka mana." Wani kallon zakuwa ga sani ya mishi yace "Oho, haka kace?" Kama rigarshi yayi ta k'asa yayi sama da uta ya zage ya rik'e a hannu, wandon ma dama k'ugunshi roba ce, sab'ule shi yayi ya bar gajeran daya tsaya mishi a cinyoyi, jefawa Amar kayan yayi wanda ke murmushi yana ayyana rashin kunyar da Amna zata gani baiwar Allah, jin kayan a fuskarshi yasa ya yamutse fuska yace "Meye haka kuma?" Saida Ammar ya zagayo ya zauna d'an nesa da Junaid da suka k'ura mishi ido yace "Ka had'a ka sanya duka, gigin tsohuwar can ya farka yasa ta mana mata a daren nan, kana so kayan bacci ma sai mun saka kala d'aya salon wata rana matarka ta k'wamuso ni a tunaninta kai ne." Jibril ne yayi dariya yace "To idan ta kama ka d'in ba sai kace mata ba kai bane." Kallonshi yayi da nufin magana amma ganin kallon da Junaid ke mishi yasa ya had'e fuska yace "Malam ko na mik'e na cire har wannan ma ta yanda za ka ga komai da kyau?" Da sauri Junaid yace "Kai wa Allah ka rufa mana asiri, ina mu ina ganin wannan al'amari, in a matse kake da kayi tsirara ka jira 'yar k'anwarmu ta zo, wannan ba laifi ba." Dogon tsaki yayi ya mayar da hankalinshi kan waya, Amar ne dake shirin fita ya cillo mishi kayanshi yace "Dan Allah ka saka kayanka, kasan fa har yara shigowa suke haka ma matan suna iya zuwa yin wani abun." Kallon Amar d'in yayi yace "To meye a ciki? Duk yaron daya ganni haka ai nima nayi zama kamarshi, kuma shima zai dawo kamar ni d'in, mata kuma da kake magana a kai duk abinda zasu gani suji kunya bai wuce wannan abun ba wanda kuma basa rayuwar jin dad'i sai dashi." Yanda ya k'arashe maganar yana nuna k'asan gajeran wandonshi da kuma had'e fuskar da yayi kai kace bashi ya fad'a ba yasa Amar cewa "Allah ya shirya ka." Ba tare daya kalleshi ba yace "Tare da ebolar gidanku ba." Jibril da tuni ya fahimta ne ya tuntsire da dariya sai Junaid da yace "Wace kuma ebola?" Jibril ne cikin dariya yace "Wa fa inba Hajia ba, nasan dai ita yake nufi." Amar ne ya d'an b'ata rai yace "Wallahi Ammar kaji tsoron Allah, ka sani fa kakar ka ce, ya zaka rainata haka?" Wani kallo ya masa galala yace "Allah ko? To zo ka ci uwani shalelen Hajia." K'wafa yayi inda Amar ya juya zai fita, muryar Ammar yaji yace "Bani kayana a hannu na." Juyowa yayi ya kalleshi yace "Kai daka cillo min a hannu na ka damk'a min? Kusa da kai fa suke ka d'auka kawai." Sake tamke fuska yayi cikin amon muryar da sam babu wasa a ciki yace "Na ce ka bani a hannu na ko." Tabbas Amar yasan inhar bai bashi ba sai sunyi fad'a, shi kuma yana so ya ga ya cika alk'awarin daya d'aukarwa Ummy na zai dinga hak'uri da d'an uwanshi dan wani lokacin al'amarinshi kamar mai aljanu yake, dawowa yayi ya d'auki kayan ya mik'a mishi kafin ya juya zai fita, kallon bayanshi yayi yace "Idan kaje ka sa mana matar nan ta rubuto maka kalar rayuwar da take so muyi da matan bayan an d'aura auren, dan mu hardace a kanmu ya zauna mana sosai." Girgiza kai kawai Amar yayi ya fice daga d'akin, d'aukar wandonshi yayi ya saka ya gyara zamanshi kamar zaiyi kwance a kujerar yana danna wayarshi yana shafar shafaffen cikinshi mai shegen fad'i, inda k'irjinshi kuma yace ja bani wuri saboda bud'ewar da yayi, jin su Junaid sunyi shiru yasa ya d'an saci kallonsu yace "Ka fad'a min indai kana sonta har yanzu ni kuma zan karb'omaka aurenta wajen iyayenta?" Kallonshi sukayi sai Junaid da yace "Ina sonta har yanzu, amma tayaya zakayi haka? Gaskiya bana son wata matsalar Ammar, kuma naga kai kan ka baka tsira ba wajen Hajia." Murmushin gefen labb'a yayiba tare daya kallesu ba yace "Ku zuba ido kuga ranar da zan fito da wacce nake so, wallahi sai dai ta ganta da ciki kawai ba tare da tasan yaushe haka ta faru ba ma, shirun da kuka ga nayi saboda bana da abin fad'a ne kamar yanda na fad'a ma ita kanta tsohuwar, Amna kuma banda wani dalili na nuna mata tsana ko k'iyayya, dama wannan kankanar ce." Shiru sukayi dan sun san baida abin fad'a kamar yanda yace, da akwai kuwa daya fad'a ko da abinda zai fad'a zai jawo kwanciyar wani a gadon asibiti. Amar na fita b'angaren iyayen ya nufa dan amsa kiran da Hajia ta masa, amma yana daf da shiga saiya samu Hamna har yanzu tana zaune tana kuka, tsayawa yayi ya sunkuya kusanta yana kallonta yace "Hamna." D'agowa tayi ta sauke matsakaitan idontaa kanshi, cikin tausasawa yace "Ke ma kina kukan zab'in da Hajia ta miki ne?" Saida ta share hawaye da hannunta cikin muryar da tasha kuka tace "A'a yah Amar, yah Junaid d'an uwana ne, ba zan k'i shi, sai dai Hajia ta ruguza min burina na zama gogagiyyar mai tsara kaya (fashion designer) da kuma zama mai kwalliya, sanin kanka ne mu mata Hajia bata yarje mana fita daga garin nan ba da sunan karatu, toya kenan idan nace zan tafi da auren yah Junaid a kai na? Ba zata amince ba, kuma gashi mun riga da mun gama magana da wani compagnie dake *Abuja* zan je a hutun nan da za ayi dan fara d'aukar darasi na kwalliya, shiyasa kawai nake kuka." Shiru yayi yana kallon yatsun k'afar ta masu tsayi da tudu wanda na kusa da babban yatsan yafi kowane tsayi, ya d'an jima a haka kafin ya mik'e yace "Kiyi hak'uri kinji, zan shiga wajen Hajia yanzu na mata magana, insha Allah burinki ba zai ruguje ba." D'ago kai tayi ta kalleshi tace "Nagode yahAmar, dan Allah ka min wannan taimakon, idan ba haka ba babu wani abinda nake so sai dai na zama matar gida nima." Murmushi kawai yayi ya d'an jinjina mata kai ya shige falon, ajiyar zuciya ta sauke dan tasan zaiyi wuya Hajia ta kasa sauraren shalelenta, indai har ya nuna hakan yake so to zata amince ko da ita ba haka ta so ba. *Fatan nasara Amar* 11/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _8_ Bud'ar bakin Raudat cewa tayi "Lahh! Ai Ammien mu tana raye, tare suka tafi basraba basraba amma ita bata dawo ba." Cike da makirci tace "Ayya kunji dad'in ku, kuna da iyayenku a raye suna k'aunar ku, sannan Allah ya muku baiwa ta daula babu abinda kuka nema kuka rasa, sannan na tabbata iyayenku suna farin ciki da junansu bare hankalinku ya dinga tashi idan sun samu sab'ani." Murmushi Raudat tayi tace "Gaskiya ne aunty, duk da iyayenmu suna yawan fad'a amma dai fad'an nasu na shirme ne, dan duk fad'an su basa awa d'aya basu shirya ba, kuma dama Ammie ita tafi d'aukar zafi." Ta gefen ido ta kalleta kafin ta d'an zaro ido tace "Kina nufin yanzu nan iyayenku suna fad'a? To akan me?" Cike da yarinta Raudat tace "Kamar yanda na fad'a miki fad'an su duk shirme ne, amma mafi aksari sunfi rigima akan kishin Ammien mu, wani lokacin kuma bamu san meke had'a su ba sai dai muga Ammie na b'uya a bayan Ammie, idan ita ta tsokani Dady kenan." Saida ta kamo hannunta tace "Kenan Ammienku batayin duk abinda Dadynku baya so?" Saida ta firfito da manyan idonta masha Allah kafin tace "Ban sani ba gaskiya, mu dai kawai rayuwar iyayenmu tana bamu sha'awa, suna k'aunar junansu sosai, suna raha da wasa a zamantakewarsu, shiyasa muma muke k'aunar su." Mik'ewa tayi tace "Aunty bak'uwa saida safe." Murmushi tayi tace "Aunty bak'uwa kuma? Ki kira ni da *Nasmat*." Murmushi Raudat ta mata tace "Nice name aunty Nasmat, good night." Da kallo kawai ta bita harta fita, tana fita ta tab'e baki tana tunano abinda ta fad'a mata, mik'ewa tayi ta cire kayanta ta fad'a toilet, ta jima tana k'arewa toilet d'in kallo ganin kamar ba wajen fitar da datti da k'azanta ba, ko bacci ya kamaka sai kayi a ciki kuma cikin nutsuwa, haka ta fara wanka kafin ta idar ta fito, jakarta da suka taho da ita ta bud'a ta shafa na shafawa ta murza na murzawa sannan ta saka rigar bacci iya gwiwa mai kyau, saida ta zauna kan gadon ta d'auko wasu magungunan mata wanda ta tanadesu dan Abbas kawai tasha sannan ta kwanta. Suna kammala cin abinci Abbas ya shirya ya tafi taron nan, awa biyu ya d'auke shi kafin ya dawo gida, ya fito a motarshi zai shiga part d'in shi a farfajiyar gidan ya ci karo da mutum, mutum ma mace cikin shirin atamfa tasha ado, wa zai gani inba Harira ba, gidan shiru alamar kowa ya kwanta sai kukan d'awisu da talo-talon dake cikin gidan an ware musu wuri na musamman, tunda ya gane ita ce kawai ya zura kai zai wuce dan haka tayi saurin cewa "Sannu da zuwa yallab'ai." Tsayawa yayi kawai ya kalleta kamar mai son gane nufinta, wani farrr ta fara da ido tana takowa cikin girgiza jikinta, tabbas kayan sun amshi jikinta musamman yanzu data yi yar k'iba sun zauna mata a jiki, kwalliyar ma ba laifi sai dai kawai in baka sonta ne zaka kushe ta, mamakin irin salon da take taho dashi yake yi harta tsaya gabanshi k'amshin turarenta da baida maraba da na 'yan bori ya daki hancinshi, muryarta ce ta dawo dashi daga d'aukaewar da numfashinshi ya kusa yi saboda bai tab'a jin turare irin wannan mai tayar da hankali ba tana fad'in "Yallab'ai, dama na ga baku dawo tare da Sameera bane, shine nace bara na jira ka dawo ko akwai abinda kake so wanda zan iya yi maka?" Kallon mamaki da kuma yaushe yarinyar nan ta haukace yake mata? Me take nufi? Sameera ce ma take kira haka babu sakayawa? Saida ya d'an ja baya sosai ya k'are mata kallo yace "Ke! Yaushe aka haifeki?" Sai kuwa Harira ta sake juya ido ba tace komai ba, dan haka yace "To ki koma ki tambaya dan kisan shekarunki da nawa ba d'aya bane, ki shiga hankalinki tun wuri, dan ruwa ba sa'an kwando bane, idan kuma baki ji ba, u wil regret it, that's my last warning." Juyawa yayi a sukwane ya shige part d'in ya barta nan, tab'e baki tayi ta juya tace "Can ka k'arata da turancinka, ni inda zaka dinga min magana ma da turancin da zanfi jin dad'i." Raihan na kwance d'aki sun gama waya da mahaifiyarta, har zata kwanta dai kuma saita turawa Abdul sak'o tana tambayar ya hannunshi? Ko ba komai yaji dad'in tambayar dan hakan na nuna ta damu dashi ne, amsa mata yayi da sauk'i, Allah ya k'ara afuwa shine abinda ta fad'a ta aje wayar ta kwanta abinta. *Washe gari* da sassafe duk yaran sun shirya suna kan dinning suna jiran isowar Dadynsu, Abbas kuma na shiryawa ya fito falonshi da niyyar fita, yanzu ma wa zai gani sai Harira wacce tunda Sameera tace mata duk aikin da zatayi b sai ya kaita ga shiga sashin Abbas ba take jin haushi, wato a lokacin da suna matsayin ma'aikata ai ita ce ma ke kula da sashin shi, kenan ita ma tana tsoron a k'wace mata miji kamar yanda ta k'wace ma Salma, dan haka yau saida ta gama kimtsa yaran da ba zasu iya shirya kansu ba ta shiga falon nashi da k'ofar ke bud'e ta falon Sameera, babu wani abu da d'akin ke buk'ata amma haka ta zage tana goge goge tana karkad'a jikinta sosai cikin doguwar rigar wani tattausan less bayan ta cab'a ado. Saida Abbas ya rintse idonshi dan yanda k'ugunta ke rausayawa abin tayar da hankali ne, gashi har shatin mazaunin pant d'inta yana hange daga inda yake, haushi da takaici ne suka sashi daka mata tsawa yace "Ke!" Harira da tuni tasan da fitowarshi shiru kawai tayi a tsora ce ta juyo juyo tana saki wata k'ara duk da muryar ba siririya bace da zatayi dad'in sauraro, ba kwalliyar fuskarta ce ta sake shiga madubin idonshi ba sai k'irjinta da rigar ta matseshi sosai yayi sama kamar zasu fito, tabbas mata bala'i ne, dan k'arfin da yaji lokacin daya mata tsawar nan tana juyowa sai yaji ya rasa kuzarin, wani bala'in sanyi ne yaji hannunshi sun mishi ya kasa d'aga su, da k'yar ya iya tattaro jarumtarshi yace "Lafiya? Meya kawo ki part d'ina?" Sunkuyawa tayi tace "Ina kwana? Kayi hak'uri yallab'ai, na zo gyara..." Bai bari ta k'arasa ba yace "Kije bana so, kuma daga yau kar na sake ganinki sashi na." Sunkuyawa tayi alamar to kafin ta nufo shi, hakan yasa ya bud'e ido yana kallonta ya ga me zatayi, kan k'aramin teburin ne ta aje k'aramar wayarta da man goge madubi, duk'awa tayi zata d'auka ta d'ago kai taga ko yana kallonta, ganin ya kawar da kanshi yasa tace "Yallab'ai na kawo maka abincin ka nan ne?" Kallonta yayi zaiyi magana kuma sai yayi shiru saboda abinda ya gani, haka dai ta k'arasa kwarkwasarta ta fita ta barshi, tsaki yayi a ranshi yana fad'in "Dole ma ta kori yarinyar nan wallahi, ba zan iya ba haka kawai." Falon Sameera ya shiga kai tsaye d'akin ta ya nufa da niyyar sauke mata bala'in da yarinyar can ke son d'ora masa, amma abun takaici saida ya kai daf da d'akin ya tuna rigimammiyar bata gari, a ranshi yace "Bata kira ni ba, nima kuma ban kirata ba, hmmm." Juyawa yayi yana fad'in Allah ya sota da rahamar da sai ya tara mata uwar gajiya, daf da d'akin da Ma'arufa take ya tsaya saboda tuna akwai bak'uwa a gidan, tunani yake ko tana nan? Ko kuma tana wajen cin abinci? K'wank'wasa k'ofar yayi hakan yasa Ma'arufa dake shirin saka kaya tace "Ina zuwa." A hankali ta lallab'o ta lek'o ta hudar dake jikin k'ofar kamar yanda sauran k'ofofin suke, saida ta dafe k'irji ta zaro ido ta fara tunanin abinyi, gamsuwa da shawarar da zuciyarta ta yanke mata yasa ta wangale k'ofar d'akin tana fad'in "Lil sis ke..." Shiru tayi da mamaki na k'arya a fuskarta na ganinshi tsaye, da sauri ya kawar da kanshi gabanshi na dukan uku uku, bai tab'a ganin matar da ba halalinshi ba daga ita sai d'aurin k'irji na towel, yau gashi ya gani da idonshi, kana gani kasan hasken mai ne dan har k'arnin mai take, amma santala santalan cinyoyin masu d'aukar hankali ne, k'arin gashin da tayi wanda ya saje kamar gashinta ya kwanta bayanta, bai sake kallonta ba illa fad'in "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un da yake yi." Ita kuma babu d'ar ko kunya a tare da ita sai sunkuyar da kai da tayi tace "Good morning sir, na yi tunanin lil sis ce, dan tun jiya ita ke kawo min ziyar." Ba tare daya kalli wajen da take ba yace "Ya k'afar taki? Ki fito ki ci abinci." Yana fad'a kuma bai tsaya jin me za tace ba ya fice da sauri, farfajiyar gidan ya fita kamar zai shiga motarshi kuma saiya tsaya, tambaya yake wa kansa me yake faruwa dashi haka yau? Sai ganin matan da babu komai tsakaninshi da su yake, Allah ya sani yanzu ya zama mai yawan buk'ata, gashi duk sun saka shi ya d'auki caji kuma maganin warakar bata nan, wayarshi ya fito da ita ya danna mata kira, a daidai lokacin daya kira Sameera kuma tana daf da shiga gidan waziri, tana ganin kiran ta tsaya ta d'auka, muryarshi babu alamar wasa taji yace "Ki bar duk abinda kike ki dawo yau d'in nan." Take ya kashe wayar dan kar ma ta samu damar yi masa gardama, ita kuma da farko ta d'auka rarrashinta zaiyi yace ta dawo, amma sai taji yace wai ta dawo yau d'in nan, mayar da wayar tayi a jaka ta shiga gidan da sallama, ba mutane a gidan sai matar kawai a tsakar gida, amsawa tayi tare da d'agowa, tana ganinta gabanta ya fad'i dan tasan ba alkairi ya kawota ba, mik'ewa tayi daga zaman da take cikin sanyin jiki tace "Hajia ke ce? Sannu da zuwa, shigo ciki." K'arasowa Sameera tayi cikin wata shegiyar tafiya, d'an takawa matar tayi tana fad'in "Bari na kawo miki..." Bata fad'a ba taji Sameera ta jawo hannunta ta dawo da ita baya, kallon juna sukayi inda Sameera tace "Da alama ba sai na fad'a miki wacece ni ba? Rabuwar mu ta jiya ba tayi dad'i ba, a dalilinki mahaifina ya tafi gida da b'acin rai, a sanadiyarki mahaifina ya kasa aiwatar da abinda yayi niyya, a dalilinki jiya na kwana da ciwon kai, a dai dalilinki ne na kwana nesa da yara na ba kuma tare da mahaifinsu ba, shin kina ganin idan ban kawo miki ziyara ba nayi daidai?" Cikin rashin gaskiya ta kalleta tace "Eh...to. Hajia duk me..ya kawo wannan..maganar kuma?" Tassssss, saukar mari kawai matar taji, take ta dafe kuncinta ta durk'ushe a wurin kanta k'asa, Sameera kuma nuna ta tayi da yatsa dan matar ba wani finta shekaru tayi ba tace " Ki rubuta ki aje, bana sakin rigima cikin sauk'i, wannan marin tun jiya na so na miki shi, amma mijina bai bani dama ba, idan waziri ya zo kya gaishe min dashi, idan kuma kin shirya d'aukar fansa sai ki sanar dashi ya shirya miki bataliya guda wacce zata d'aukar miki fansar." Tana gama fad'a ta juya ta fita a gidan hankali kwance, mik'ewa matar tayi tana mamakin k'arfin halin Sameera, amma kuma kamar yanda tace ba shakka zata d'auki fansa ko da ba a kanta bane, tasan shirin da suke da shi a k'asa dole zai gigita duk wani makusancin sarki da ma iyalinshi, dan haka tayi k'wafa ta shiga harkar gabanta ba tare da tunanin fad'awa ko da wazirin ba bare wani, ita kuma tana fita daga nan masarauta ta shiga, a cikin fada aka basu wuri ita da Imran suka tattauna akan maganar aurenshi, ta jima suna hira tana bashi shawarwari kafin ta mishi sallama ta fito, tana dawowa tamasal ta fara had'a nata kayan dana Abbas dan shi ma bai d'auki komai ba, amma kuma sai kawu Bakura ya dinga nemanta da shawara kan bikin Husna, a k'arshe dai saida suka tafi da *Jebu* da kuma Husna ta zab'i kayan da take so kafin suka dawo, sai bayan sallah la'asar ta shirya ta zo airport inda ta samu tunda sukayi waya da Abbas ya turo da jirgin da zai d'auke ta, tana shiga suna kimtsa suka lula sai Abuja kuma. Tun lokacin da sukayi waya ya tura a d'aukotaya zuba ido yana jiran isowarta, yara ma da zasu tafi islamiyya sai nan suka shigo suka gaishe shi, haka yake zaune yana duban agogo, daya ga hakan ba zai gyara shi ba saiya kira captain Ali ya tambaye shi, a cewar shi har yanzu madame bata k'araso ba, nan ya kashe wayar yayi cilli da ita ya kuma niyyar ba zai kirata ba sai ta zo kawai, yana zaune ya jingina sosai a kujerar kamar mai bacci ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yaji an turo k'ofar an shigo, in dai ba Sameera ba Ammie ce kawai keyi masa haka, dan haka bai damu ba sai bud'a idon da yayi kawai, Ma'arufa ce wacce ta ga motar shi alamar bai fita ba kuma basu ci abinci tare da shi ba, d'auke take da babban faranti da chips a ciki da soyayyar plentain, sai fresh milk kamar yanda Razeena ta fad'a mata, saida ta rufe k'ofar d'akin sannan tayi sallama cikin murya mai ja hankali, da sauri ya sauko kanshi izuwa k'asa dan jin ba muryar Ammie bace, saida gabanshi ya fad'i lokacin da suka had'a ido, yana mamakin dalilin da yasa yake jin mummunan fad'uwar gaba idan ya ganta, bai iya d'auke kanshi daga kallonta ba har saida ta sunkuya ta aje farantin akan k'aramin teburin ta d'ago tace "Barka da hutawa yallab'ai, munga shiru har yanzu baka fito bane yasa na kawo maka wannan." Jawo mishi teburin tayi gabanshi yana kallonta ta zuba komai kuma yanda ya dace kafin ta kalleshi tace "Aci lafiya." Da kallo ya bita harta fita ta na d'an d'yangasa k'afar ta a hankali, saida ta fita yake mamakin rashin kunyar yarinyar, anya kuwa idan yar mutumci ce zata iya yarda su had'a ido bayan ganin daya mata d'azu? Abune mai kamar wuya gaskiya ga mace mai kunya, tab'e baki kawai yayi ya k'ara janyo table d'in ya soma cin abincin. *Yanayin* mai matuk'ar dad'i, mai kula da gidan yayi aikinshi ta hanyar share furen flawer's d'in dake zuba, ya gyara wasu flawer's d'in ta hanyar rage musu girma da basu ruwa, a hankali iska ke kad'awa yana fito da wani daddad'an k'amshi da sanyi mai ni'ima, Saleem ne zaune a cikin mota ya gama rabawa duk yaran chocolat, saida zasu shiga ciki ya kalli Khalifa da shi yanzun yake ganin ya girmi chocolat yace "Idan ka shiga ciki kace Raihan ta zo ina son ganinta." "To." Ya fad'a yana bashi hannu ya shiga ciki, tunda ya shiga ya samu Raihan a kicthen tana had'a cake wanda ta gani anyi a tv, dayake yarinya ce mai k'ok'ari kuma uwarta ta d'ora ta tun tana k'arama yasa yanzu haka dai bata da matsalar girki, yana zuwa yace "Aunty Raihan uncle Saleem ne a waje wai yana jiranki." Kallonshi tayi ta d'an yi shiru kafin tace "Ka fad'a masa ina aiki, i'm busy." Wani kallo ya mata yace "Wai ke me kike nufi ne? Haka ma ranar nan yace ki zo kika ce wai kina aiki." Cikin taushin murya da sanyin hali tace "To ba aikin nake ba? Dallah malam kaje ka fad'a masa ina aiki." Juyawa yayi zai fita yana fad'in "Ni yaronki ne to da zaki aike ni? Ke kije ki fad'a masa." Kallonshi tayi tace "Haba yaro ba laifinka bane da ka raina ni, Dady ne yake nuna maka kaine namiji dan haka har ni zaka iya mulka, amma ba komai its not ur fault." Khalifa kam da son girma fa bai zo fad'awa Saleem sak'on Raihan ba, sai Raudat dake zaune falo yace ta je ta fad'a masa, tashi tayi tana turo baki dan ita kuma a nata b'angaren gani take mugun raini ne ace Khalifa ke gaba da ita, kasancewar jikin Abbas Abbas ne da ita na girman k'asusuwa yasa har gabanta ya fara tara nonuwa, tana fad'a masa ita ma ta dawo falon ta zauna, Saleem kuma k'wafa yayi yace "Ba zan tab'a barinki ba, dole sai plan d'ina ya kammala a kanki, stupid girl kawai idiot." Harya zura k'afafunshi zai rufe motar yaji ance "Idan har kana so ka samu shiga kar ka zama lazy man, confidence kake buk'ata kafin samun zuciyar Raihan." Juyowa yayi yana kallon Fadila dake tunkaroshi, ba laifi ita ma kyakyawa ce, bai daina kallonta ba har saida ta k'araso ta tsaya kusa da shi, kafin yace wani abu tace "Tun ranar can na hangi zunzurutun k'aunar da kake mata, amma ita d'in yarinya ce da ba komai ke zama a kanta ba bare tayi tunani a kanshi, amma idan zaka kama k'afa dani burinka zai cika akan Raihan." Wani shu'umin kallo ya mata da murmushi a gefen lallab'anshi irin na tarkona ya kama kurciya, ita ma kallonshi take tana ganin nata burin zai cika idan tayi k'ok'ari ta had'a soyayyarsu, cikin kwanciyar hankali yace "Are u sure zaki taimaka min har nayi winnen heart d'in ta?" Cike da k'warin gwiwa tace "Ina baka tabbacin haka." K'aramar yatsarshi ya mik'o mata tare da fad'in "Mun kulla daga yanzu kenan? Mun zama friends." Bata bashi yatsanta ba sai kai data jinjina masa alamar eh, fitowar Abdul a sukwane daga part d'in yasa hankalinta komawa can, bata jira ya nemeta ba ta taka da sauri ta tarbeshi tana fad'in "Yah Abdul ina zuwa haka da yammar nan?" Cikin sakin fuska yace "K'anwata zanje wani wuri ne, ko kina zuwa ne?" Cikin salo kamar babbar mace tace "Yah Abdul tafiya indai tare da kaine zan yarda na shekara dubu ina yinta ba zan gajiya ba ai." Murmushi ya mata yace "To nagode k'anwata, yanzu dai zan tafi saina dawo, ko da wani geft kike so na siya miki?" Saida ta kashe masa ido tace "Kawai ni ka kular mana da kanka." Nan ma murmushi yayi yace "I wil insha Allah, bye bye." Yana fad'a ya shiga motarshi ya tayar, da kallo ta bishi harya fita daga gidan kafin ya kula da Saleem wanda shima kallonta yake ya hango soyayyar Abdul a idonta, k'arasowa tayi hakan yasa ya mata dariya yace "Kina ta so ki b'oye, amma kuma zuciyarki da idonki sun k'i lamuntar hakan, meyasa zaki cutar da kanki ta hanyar hana zuciyarki abinda take so?" Kallonshi tayi sosai tana nazari, ko ba komai yau ta samu wanda ya gano abinda ke zuciyarta, dan haka babu fargaba cikin rufewar ido tace "Saboda ba ni ce na dace da shi ba." Da mamaki yace "To wa kenan ta dace da shi?" Kai tsaye tace "Raihan mana." Yanda ta fad'i sunan a take saiya hangi kamar zuciyarta ta fara tafasa, dan ya samu biyan buk'ata sai yace " Amma ke ma mace ce mai class , kina da kyau ilimi da wayewa, sannan iyayenki babu na yarwa, so meye wata 'ya mace zata nuna miki har ta hanaki cikar burinki?" Shaid'an ne ya dinga hura wutar dake zuciyarta harta saki baki tace "Ban sani ba nima, amma ko Ummata sau da dama zaka ga tana nuna banbanci tsakani na da ita, haka ma Abbana yana fifitasu a kanmu, gaba d'aya mun zama kamar wasu bayinsu, mahaifinsu ne ke juya namu iyayen, mahaifiyarsu ma ta mulki iyayenmu, hatta makaranta wannan sai a motarsu ake kaimu alhalin iyayenmu nada halin siyan motan da tafi tasu." Harira ce ta fito farfajiyar gidan tana waya da Adamu yayanta, hakan yasa Fadila yamutsa fuska tace "Ina ga zamuyi magana da kai, yan sa ido sun fara fitowa." Wayarshi ya mik'o mata yace "Give me ur phone number, i wil call u." Karb'a tayi ta saka mishi ta mik'a mishi tayi gaba, shima fita yayi daga gidan, zata shiga part d'in Sameera ta hangi Abbas da fitowarshi kenan daga wanka ya haura sama dan ya ga ko motar da zata kawo mishi matar shi ta si, ganin babu motar yasa shi ciro wayarshi ya dannawa dr Kabir kira, a lokacin kuma Fadila ta zagaya ta haura ta saman dan ta gaishe shi su kuma yi hira kamar yanda suka saba, duk da yanzun tana jin ba zata tsaya yi hirar ba dan Saleem ya tsokano mata wani abu shaid'an kuma ya sake zugata, sam baisan da zuwan mutum ba hasalima baya tsammanin zuwan kowa wurin, tambayar dr Kabir yake yaushe result d'in Abdul zai fito yaje ya karb'a, bayan ya fad'a masa ne Abbas d'in ke cewa "Ina fatan kar a samu kowace cuta a jikinshi, dan in aka samu tofa babu maganar aure tsakaninshi da Raihan, dan su Abba ba zasu bari ba, sanan dan Allah ka k'ara rik'e mana sirrin nan ko Abdul kar yaji an mishi gwajin nan bare kuma wani nashi." Alk'awari ya mishi yace ya kwantar da hankalinshi, Fadila na jin haka tayi saurin komawa ta sauka k'asa, ranta ne ya sake b'aci sosai tana ganin kenan shi kanshi Abdul d'in ma basu raga ma ba, ai kuwa shiryawa tayi zata bayyana mishi soyayarta in ya so duk abinda zai faru ya faru. Ta sauke kenan aka bud'e gate d'in gidan motar Abdul ta shigo tare da Sameera, dama saurin da yake zaije d'aukar ta ne, Abbas na hangensu har Abdul ya shiga da jakarta ita ma ta bi bayanshi, fita yayi daga nan yasa makullinshi ya bud'e d'akin ta ya sake rufe k'ofar da makullin ya zage shi, ya kusan minti talatin a d'akin ko hasken fitila bai kunna ba kafin yaji Sameera ta taho cikin d'aga murya tana fad'in "Ku wa Allah ku wa ubanku ku barni nayi wanka zan fito yanzu." Yana jin ta saka makulli ya taso daga kan gadon ya lab'e jikin k'ofar, tana bud'ewa ta mayar ta rufe da niyyar shiga wanka, ta juyo kenan da nufin kunna hasken d'akin taji an cakumeta ta baya tare da rufe mata baki da hanci da tafin hannu lallausa wanda hakan yasa k'arar da tayi bata fito ba, tabbas tasan Abbas ne amma me yake nufi da haka bata sani ba? Take a wurin gyalenta da d'an kwali ya fita ta saki jakar data shigo da ita, ta bayanta ya d'ora hab'arshi a kafad'arta yace "Wato a gabana kike zagar min yara ko? Saboda kina tunanin bana gidan, ashe dama haka kike tsine min bayan ido na? To bari kiga yanda zanyi dake." Cillata yayi akan gadon ya kuma bita ya taushe yana fad'in "Jiya nace ki zo, amma ki ka k'i zuwa dan kin raina ni, sannan kika cije ni nace zan rama kika ce na rama d'in, to bari kiga ikon Allah Sameera, ba dai dan kinga ina jin tausayinki ina d'aga miki k'afa ne yasa kika raina ni ba." K'wafa yayi yasa k'arfi ya cire zip d'in rigarta da k'arfi, bata fara jin tsoro ba har saida taji ya rabata da komai na jikinta, da k'arfi ta k'walla kiran "Ammieeeee!" D'aga hannu yayi kamar zai mareta yace "Wallahi kika k'ara d'aga min murya saina zabgeki da mari, fitsararriya kawai." Yana fad'a ya fizgi k'afar ta da k'arfi babu alamar tausayi ya wareta, sake fashewa tayi da kukan shagwab'a tare da rufe kumatunta karya mareta, ai da iya k'arfin da Allah ya hore masa ya zage ya saisaita kansa zuwa hanya madaidaiciya ya durmiya cikin jikinta, rad'ad'in azabar da bata tab'a ji bane ya ziyarce ta lokaci d'aya, rikid'ewa idonta sukayi ta bud'a gaba d'aya bakinta zata saki k'ara yasa hannu ya rufe mata bakin... *Takwara maganinki kenan ai😡* 12/06/2020 à 11:17 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _7_ Da sauri Abbas ya rik'o ta dan yasan me zatayi, juyowa tayi ta kalleshi ganin ya had'e rai sosai yasa ta fincike daga rik'on daya mata ta fice a falon da sauri tana hawaye, girgiza kai yayi yana sake jadadda kai kukanshi ga ubangiji akan Allah ya sanyaya mata zuciyarta, cikin sanyin jiki ya zauna inda Abba ya kalli uwar d'aki data fara magana kamar haka "Amma yallab'ai sai naga kamar gaskiya matar waziri ta fad'a, dan ko ni dake uwar gidan takawa kuma uwa ga sarkin yanzu bansan da wannan magana ba, amma abun mamaki wai har kuna cewa ma burinshi kenan." Kallonta Abba yayi, shin nesan da sukayi da juna na tsawon lokaci ne yasa *Hafsatu* mantawa da waye shi? Ko kuma sanyin da yayi ya rage tijara ne yasa har zata iya kallonshi ta fad'a masa wannan maganar? Wane irin raini ne wannan suka d'ora mishi haka harda matar da bai ma gama saninta ba ko a fuska? Me zaiyi musu ne ma wai? Ya jima yana mata wannan kallon mai tattare da nazarin abinda zan fad'a miki kafin ya nisa yana kallonta ido cikin ido yace "Hafsatu kinsan dai da nine a gaba da mijinki ko? Sannan kinsan da mijinki ma kallo na yake kamar mahaifi tun bayan rasuwar iyayenmu? Sannan nasan kinsan cewa kaf yaranshi ina da hakk'in da zan iya yanke hukunci a kansu ba tare da sanin shi kanshi margayi ba? Dan haka ki saurara min tare da d'aga min k'afa, kar kisa nayi abinda za'a buga sunana a mujalla shafi na farko da zata fito safiyar gobe." K'wafa yayi tare da juyawa ya kalli liman yace "Liman, kana da wata matsala idan aka d'aura auren nan a yau?" Girgiza kai yayi yace "Babu ko d'aya ranka shi dad'e." Imran ya kalla yace "Kai fa Imran? Kana da matsala da hakan?" Shi ma girgiza kai yayi cikin ladabi yace " Babu Abba." Mik'ewa yayi tsaye tare da fad'in "Duk mai farin ciki da auren nan ya fara shiri yanzun nan, dan ana idar da sallah la'asar zan d'aura auren Imran da 'yar wajen liman Safiyya." A wannan karan kam uwar d'aki ba wai tsananin son da take sai Imran ya auri 'yar waziri bane yasa ta shiga rud"u da firgici illa yanda take ganin za'a nuna mata iko da d'an data haifa, kuma wai ba ma uban daya haife shi ba, wannan ne yasa ta mik'ewa ita ma kamar zararra tace "Me? Aure? Zaka wa d'an nawa ba tare da amincewata ba? Wallahi baka isa ba, *Mus'ab*, karfa kaga muna d'aga maka k'afa, can ma kawaici ne a matsayinka na yayan mijinmu, amma ka sani shi kanshi yanzu baya raye, dan haka wallahi ba zan tab'a yarda ka had'a auren Imran da wannan yarinyar ba yar matsiyata, indai ni na haifi Imran kuma ta hanyar aure." K'arama a cikin matan takawa ce ta kalleta a nutse tace "Haba uwar d'aki, sai naga kuma ko takawa baya raye ai akwai alak'ar data had'a ki zumunci da danginshi ko da kuwa ba kya so, wannan alak'ar kuma ita ce 'ya'ya, ki nutsu dan Allah sai a bi komai..." Da hannu ta dakatar da ita da cewa "Dakata min malama, 'yan bak'in ciki kawai, ai dama nasan ba son yaya na kuke ba shiyasa hakan ba zai dameku ba, to ke ki bada d'an ki mana sai a had'a shi da wannan bak'in irin, amma ba ni ba." Imran da tunda ta fara magana yake kallon yanayin Baffan nashi, sai jimk'e hannunshi na hagu yake yana ji kamar zai kai duka, inda yake d'an lumshe idon shi yana bud'ewa duk da haka saida sukayi ja, yasan zaman nan ba zai k'are musu da kyau ba, dan haka ya kalli uwar d'aki a sanyaye yace "Umma, dan Allah ki zauna muyi magana." Cikin b'acin rai tace "Wane zama kuma zanyi, Imran a gabanka za'a tozarta mahaifata a nuna min ban isa da kai ba, aure? Ka manta aurenka na farko ma haka aka d'aura maka shi ba tare da ina so ba, shine yanzu ma zaka sake wani auren saboda mahaifinka, me kake so da ni? Kana so dole saika nuna min ka fi son mahaifinka a kaina? Imran uwa fa ba wasa bace, karka manta da haka, amma idan kace zakayi to ba zan hanaka ba, kaje kayi ga wurin nan." Cikin tsananin rashin jin dad'i ya d'an girgiza kai, har zuciyarshi yana son auren yarinyar baisan me yasa ba, ga kuma abinda mahaifiyarshi take fad'a, d'agowa yayi ya kalleta a nutse cikin taushin murya yace "Umma, wallahi ba wai na fifita Abba a kanki bane, ba kuma zan bi umarninsa bane dan na b'ata miki rai, wallahi ni da kaina na shawarci takawa akan maganar auren da nake so na k'ara, kuma shi ya bani shawara ga 'yar liman nan, nasan ba zai min zab'in da zai cutar da ni ba shiyasa ma na amince da gaggawa, amma ina neman afuwarki idan ranki bai miki dad'i ba, kuma duk da haka ina rok'on alfarmarki da ki barni nayi auren nan Umma, shine cikar burin takawa, Umma idan kina so ma zaki iya bani wani umarni kema na miki alk'awarin zanyi duk abinda kika saka ni indai bai sab'awa shari'a ba." Duk maganganunshi babu wanda ya shigeta bare har yayi tasiri a zuciyarta, amma kam maganarshi ta k'arshe tayi armashi, dan haka ma ta d'an saci kallon liman da shima ya kalleta a fakaice sukayi murmushi, saida ta gyara tsayuwa tace "Ka tabbatar zakayi duk abinda zan saka ka?" Da ladabi yace "Eh Umma, insha Allahu zanyi indai baifi k'arfi na ba." Kallon Abba tayi wanda ke tsaye yana kallon ikon Allah kafin ta kalli sauran kishiyoyinta, tab'e baki tayi sannan ta kalli Imran tace "Ina so ka auri 'yar waziri." Da sauri Imran ya k'ura mata ido yana kallo, liman ya kalla ya kalli Abba dake tsaye har yanzu, kallon waziri yayi tare da matarshi da ya ga ita tuni harta washe hak'ora, a cikin ranshi kawai ya furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Allahumma ajirni fi musibati, wak-lufli khairan minha." Kallonta yayi yaga ta kafeshi da ido, babu yanda zaiyi haka yace "Na amince Umma, Allah yasa hakan ya zama alkairi a gare ni." Sai lokacin ta nutsu ta zauna tana kallonshi tace "Kaga kenan sai a d'aura auren tare ko?" A hankali ya kalli Abba da kamar ka k'yarta mishi ashana ya kama da wuta, d'auke kanshi yayi daga kallonshi saboda tsoro da kwarjini ya kalli liman, cikin girmamawa yace "Ku gafarce ni Liman, idan babu damuwa ko za'a iya d'aga auren nan har nan da sati d'aya, dan bana so daga rasuwar takawa ace nayi aure kuma har mata biyu a lokaci d'aya." Da fara'a liman yace "Babu komai mai martaba, wannan ma shawara ce mai kyau, sannan sati kamar gobe ne idan da rai da lafiya, Allah dai ya nuna mana yasa alkairi." Haushi ne yasa Abba barin falon rai b'ace inda Ammie ta bi bayanshi, harsu Imranatu da su Naseer ma bin bayansu sukayi, Abbas ma cikin kamala ya fita tare da Imran d'in inda suka k'ara tattaunawa akan lamarin, daga nan shima gidan kakannin na su ya nufo wanda suka rasu shekaru da suka wuce yanzu sai yan uwan mahaifiyarsu ne a gidan da iyalensu, tun a k'ofar gidan ya had'u da Abba da su Bashir cirko cirko suna kallon Abba daya jefa jakarshi a mota, da mamaki Abbas ya kalli Ammie da ita ma take kallonshi jiki a sanyaye yace "Ammie lafiya? Ba dai tafiyar ce ba?" Cikin k'asa k'asa da murya tace "Nima tun d'azu abinda nake tambaya akai kenan ya min shiru." Abba daya rufe boot d'in mota zai shiga mazaunin matuki ne yace "Duk mai tafiya ya zo mu tafi, wanda ba zashi ba kuma saiya zauna." Aabbas ne yayi saurin cewa "Abba ka barshi to zan tuk'a mu zuwa airport d'in, bara na kira Sameera." Da sauri ya shiga kai tsaye kuma d'akin da suke sauka ya wuce, kwance ya sameta akan gado, shi farko ma mamaki ta bashi daya ganta wai tana kuka, amma da yaji harda shashek'ar kuka take wai ita an mata magana sai ta ma bashi haushi, daga k'ofar d'akin yace "Malama ki taso mu tafi idan kin gama kukan to." Shiru tayi kamar ba tasan ma dashi a wurin ba, cikin dakakkiyar murya yace "Nace ki taso mu tafi ko, Abba ne a waje ke jiranmu fa, kinsan kuwa a kan ki ba zan yarda na sake b'ata masa rai ba." Ai kamar jira take sai ta d'ago cikin kuka ido sun mata jawur tace "Sai ka tafi mana, kasan ba zaka b'ata masa rai a kaina ba meyasa ma ka zo inda nake, ku tafi ku barni babu inda zanje ni." Ko takalmi bai cire ba ya shigo d'akin ya d'auki gyalenta dake kan gadon ya rik'e d'aya hannun kuma ya kama damtse ya jata, tuburewa tayi tana fad'in "Wallahi ka sake ni, ka rabu dani na fad'a maka babu inda zanje fa." Har sun fito fili gidan taga da gaske janta yake sai kawai ta kalli hannun nashi ta sunkuya ta gartsa masa cizo *(karo na biyu kenan😁)*, Abbas da saukar hak'oran kawai yaji baisan sanda ya saketa ba yace "Ashhhhh." Kallon hannun yayi har jini ya kwanta abinka ga farar fata, a fusace ya kalleta da niyyar zabgeta da mari ma'ana tarihi ya sake maimaita kansa, sai kawai ta zabga da gudu ta koma d'akin ta mayar da k'ofa ta rufe, cikin k'arajin murya take fad'in "Na ce ba zanje ba, ka rabu dani mana ko ana dole ne?" Dafe k'ugu yayi ya sauke ajiyar zuciya, a ranshi yake ayyana gaskiya badan suna cikin mutane ba, to fa daya b'alla k'ofar nan yau saiya tab'a lafiyar jikinta, dan har yanzu tana wasu abubuwan ne saboda tab'arar da ita da Ammie keyi, amma ba dan haka ba ai abinda tayi yanzu ko Raihan tayi shi saika mata tsinannen duka bare ita uwarta, wata uwar oda da Abba yayi daga waje yasa Abbas zabura ya juya ya kalli k'ofar, sake dawo da kallonshi yayi ya ga k'ofar a rufe, matsawa yayi jikin k'ofar yace "Zan tafi, idan kinga dama ki tabbata a nan, amma ki sani cizona da kikayi bashi kika d'auka kuma zan rama." Daga cikin d'akin tace "Ka rama mana, ko kashe ni zakayi ba zanji ciwo ba indai har zaku tafi ku barni, dan wallahi saina ci uwar matar nan ko kuma na k'ona garin nan." Wata zuciyar ta fad'a mishi hushi ba naka bane tunda kasan halin kayanka, a hankali ya saisaita nutsuwarshi ya d'an had'a kanshi da k'ofar d'akin yace "please Sam kar kiyi abinda bai dace ba, dan Allah na rok'e ki, kinji." Cikin kukan daya tabbatar daga zuciyarta yake tace "Ba zan iya ba Abban Ameer, matar nan fa mahaifina ta kalla ta fad'a mishi mak'aryaci, kana ganin na zama 'yar halak idan har na rabu da ita?" Wata odar ya sake ji wacce ta sashi sake fad'in "Meera ki bud'e k'ofar nan ki fito mu tafi, Abba yana jiranmu kuma kinsan shi ma ranshi a b'ace yake." Ba tare data daina kukan ba tace " Ba zan biku ba Abban Ameer, kawai ku tafi ku barni anan." Yasan tunda ta fara ba zata sauko da wuri ba, gashi kuma har ga Allah shi ma baida niyyar sake kwana anan saboda akwai muhimmin zaman da zaiyi a daren yau d'in, dan haka yace "Shikenan zan tafi na barki anan, amma ki min alk'awarin ba zakiyi fad'a da matar nan ba." Shiru tayi sai kukan da take rerawa har yanzu, a hankali ya sake cewa "Please, do it for me, karki manta cewa ni mijinki ne, sannan kin min alk'awarin yin duk abinda zai faranta min raina." Har yanzu shiru babu alamar zatayi magana, dan haka ya juya ya fita yana sake tattare gyalenta dake hannunshi, yana zuwa Abba bai bari ya amshi tuk'in ba, saida suka fara tafiya Ammie ta tambaya ina autarta? Yana fad'a mata tace ba zata taho ba ta kalli dake tuk'i kamar zaiyi ihu tace "Dan Allah ka aje ni na koma wajenta, gobe saimu dawo tare da ita." Wani wawan birki ya taka daya sa su tsorata, sauke jajayen idonshi yayi a kanta wanda yasa gabanta dukan dubu uku uku, da sauri tayi k'asa da kanta hakan yasa Abba cewa "Ki zab'a to, idan har na ajeki anan sai dai kuyita zama ke da ita, tunda abun na ku iskanci ne." Tun daga lokacin babu wanda ya sake magana a cikin su har suka isa airport suka shiga jirgi suka sake d'agawa, a haka suka kai gida tafiyar babu dad'i ko kad'an. *Bayan tafiyarsu* Tun bayan tafiyarsu da kwana biyu Ma'arufa da Ma'aruf suka zo Abuja a motar abokin Ma'aruf, shi da kanshi ya zo har k'ofar gidan wajen mai gadi yake tambayar ko yallab'ai yana nan? Kasancewar abubuwan da suka faru yasa Abbas d'aukar ma'aikata wanda suka san aikinsu yasa mai gadin cewa "Lafiya kake neman Alhaji?" K'aryar da yayi cewa shi yaron yallab'ai ne yasa mai gadin cewa "To ka kira shi mana kaji inda yake." Cikin son lauyewa yace "Eh kuma fa hakane." Daga haka ya juya ya bar k'ofar gidan, amma rashin sanin inda zai samu bayani akan Abbas na gari ko bayanan yasa ya fara sintiri a unguwar dan sanin ta yanda zasu fara, yana ganin lokacin da aka fita da yara idan zasu tafi school kuma yana ganin lokacin dawowarsu, haka kuma yana ganin shigar Saleem gidan wanda a wannan lokacin ke yawan sintiri gidan duk dan son samun kusanci da Raihan, idan zai zo haka yake kashe ma su Khalifa kud'i sosai sannan ya kawo musu da sunan tsaraba, faran faran yake nuna musu a fuska yayin da k'udirinshi kuma mummuna ne, kuma duk wani motsinshi Fadila ita ma a hankalce take da shi, sai dai har yanzu Raihan ta k'i yarda su keb'e daga ita sai shi bare harya fad'a mata wani abu da zai sa ta fahimta, a hakane washe gari kwana uku sai ga motar su Abbas sun dawo daga basraba wanda hakan ya wa Ma'aruf dad'i kuma ya hanzarta zuwa ya d'auko Ma'arufa a gidan da suka sauka. Yaran sunyi farin cikin dawowar iyayensu da kakaninsu, amma basu ji dad'i ba da aka ce musu mahaifiyarsu bata taho ba, bayan sallah magriba Abbas ya shira tare da Abdul suka fita a motarshi, duk da yana sauri ya dawo dan akwai taron da zai shiga da compagninshi na motoci k'arfe *09:00* am saboda wasu manyan bak'in da suka zo bai hanasu tafiya a hankali ba suna hira, cikin minti ashirin suka isa asibitin kud'i wacce d'aya daga cikin yaran *ABBASIYA* ne mamallakinta, bayan sunyi parking ne Abbas ne ya kalli Abdul yace "Ka jirani ina zuwa." Cikin mamaki da fargaban abinda ya kawosu asibiti Abdul yace "Dady lafiya ko? Waye ba lafiya? Kai ne?" Murmushi ya masa yace "Bani bane, kuma kowa lafiyarsa k'alau, kawai dai na zo ganin wani ne a ciki." Saida ya sauke b'oyayyar ajiyar zuciya yace "Ok Dady, a fito lafiya." Jinjina kai yayi ya fita daga motar ya shiga ciki Abdul na kallonshi harya b'ace mishi, bayan ya shiga ne yake fad'awa *Dr Kabir* sun zo tare da yaron da za mishi gwajin jini, kuma kamar yanda ya fad'a baya so yasan da an deb'i jininshi ne dan ayi wani abu da shi, saida ya sake tabbatar mishi da babu matsala, saida yayi kira a waya ba jimawa ya datse kiran kafin suka fito tare, Abdul na ganinsu ya fito daga mota cikin girmamawa ya gaishe da Dr Kabir, amsawa yayi cikin raha kafin Abbas ya kalli Dr Kabir yace "Muje na gani ko?" Da girmamawa yace "Yes sir, zamu iya tafiya." Wani b'angare na musamman suka nufa inda Abbas yace Abdul ya zo su tafi, suna cikin tafiya wani mutum ya fito daga cikin gurin da zasu shiga, saidai mutumin a matuk'ar firgice yake wanda zaka ita gani k'arara, suna kusa da juna shi da Abdul sai kawai yayi saurin dafe hannunshi tare da sakin 'yar k'ara, da sauri Abbas ya rik'e shi yana kallonshi yana fad'in "Son lafiya? Meya faru?" Murmushin yak'e yayi yace "Nothing Dady, wani abu ne naji ya soke ni a hannu na." Ya fad'a yana d'aga hannunshi tare da kallon wurin, da sauri dr Kabir ya matso yana fad'in "Oh my goodness, yana zubar da jini fa." Juyawa Abbas yayi ya kalli mutumin da yayi kamar baisan tsiyar da suke ba saboda tafiyarshi kawai yake, da nuna reaction d'in takaici yace "Kabir waye wannan? Ina kuka samu mahaukata irin haka?" Cikin jimami dr Kabir yace "Sorry sir, maybe ko ya karb'i result d'in shi ne kuma sakamakon ciki ne ya d'aga mishi hankali, ko kuma dai wani ne babu lafiya ana neman jini ba'a samu a lab d'in mu ba." Kama hannun Abdul yayi suka shiga ciki da niyyar ya duba shi, suna shiga ya zaunar dashi akan kujera, wata yar roba ya d'auko mai haske wacce tsayinta ba zai wuce d'an yatsa manuniya ba ya tara jinin, Abdul na kallo baiyi tunanin komai ba, saida ya gama ya shafa mishi magani a wurin tare da rufe mishi ciwon dan dama komai a tsare take ba wani babban ciwo bane, fitowa sukayi duk da haka saida ya bashi magani dan kawar da duk wani zargi yace yasha saboda kar yayi zazzab'i ko hannun yayi kumburi, a haka suka d'auko hanyar dawowa gida, wannan karan Abbas ne ya tuk'a motar har suka iso layinsu. Kamar yanda Salma ta fad'a musu haka suka aiwatar da komai, Ma'arufa na ganin motar Abbas ta danno cikin layin ta taho a guje ta shiga gaban motar har saida ta bugeta kuma taji zafi, take ta fad'i a wurin tayi kamar ta suma amma tana jin duk abinda zai faru, jakar kayan dake hannunta ce ta fad'i gefe, inda d'an kwalinta kuma ya rufe mata fuska, cikin tashin hankali Abbas ya fito tare da Abdul suna salati da sallalami, suna zuwa gaban budurwar da ke kwance suka ganta kamar babu rai, amma kuma babu alamar rauni a jikinta ko d'aya, a hankali Abdul ya sunkuya yana kiran " Baiwar Allah, baiwar Allah kinji ciwo ne?" Jin shiru yasa Abbas d'agowa ya kalli Abdul sukayi ido hud'u yace "Ko dai ta mutu ne?" Ido waje Abdul yace "Ban sani ba Dady, mu kaita asibiti to." Da sauri ya d'ago ya juya ya ga babu alamar mutane a wurin dan unguwar silent ce, dan haka ya tak'ark'are zai kamata yace wa Abdul "Help me mu sata mota." Da sauri suka kamata suka nufi mota da ita zasu saka ta gidan baya, k'aramin kallabinta ya fad'i k'asa fuskarta ta bayyana, dammm! Abbas yaji gabanshi ya fad'i saboda kallon fuskarta da yayi, har suka sakata a ciki Abdul ya d'auko jakarta Abbas bai daina kallonta ba, tabbas babu kama a fuska, amma dai yana jin kamar zai tuna wani abu a game da yarinyar, wani yanayi yake ji da bai iya fad'in takamaimai abinda yake ji ba lokaci gida, har Abdul ya saka jakarta bayan inda take zaune ya rufe Abbas na tsaye, Abdul ne yace "Dady ko ka santa ne?" Da d'an sauri ya kalleshi, maimaita tambayar yayi a ranshi *ko na santa?* to a ina? Ya tambayi kanshi, cikin sanyin jiki da rashin kuzari ya rufe motar hakan yasa Ma'arufa farkawa, a zabure, saida ta juya da k'arfi ta ganta a mota sai kawai ta fashe da kuka da k'ok'arin bud'e motar tana fad'in "Wayyo Allah na shiga uku, dan Allah ku rabu dani karku cutar dani, dan Allah kuyi hak'uri kunji ku sauke ni anan, zan koma gidanmu ma." Jin ta bud'e motar yasa su zagayawa wajenta da sauri suna son suji akan su wa take magana, fitowa tayi amma saboda iya shege saita durk'ushe alamar k'afar ta ba zata taku ba, Abbas ne yace "Kinga baiwar Allah, ki nutsu ki kwantar da hankalinki, babu abinda zamu miki, asibiti ne zamu kaiki kinji." Sake mik'ewa tayi tana kuka tace "A'a wallahi bana so, dan Allah ku barni na tafi kafin su riskeni a hanyata, wannan ba komai bane a wajena, nasha wahalar da tafi wannan ma kuma ban mutu ba." Zata taka k'afar ta sake cijewa ta d'yangasa ta da k'yar tana cije baki, lura da hakan da Abbas yayi yasa yace "Saurare ni baiwar Allah, da alama k'afar ki ta bugu sosai, ki zo mu kaiki asibiti daga nan saiki fad'a mana inda zaki je sai mu kaiki." Kamar gaske cikin kuka mai ban tausayi tace "A'a ba zanje ba, dan Allah ku barni na tafiya ta, na so ace had'arin nan da mukayi da ku ya zama silar mutuwa ta, amma gashi har ita kanta mutuwar ma bata son d'auka ta, ya Allah! Sai yaushe ne wannan azabar zata yaye?" Yanda take magana da kuma yanda take rera kukan yasa jikinsu duk yin sanyin, a hankali Abbas yace "Baiwar Allah yanzu ina zaki je?" Girgiza kai tayi tace "Ban sani ba." Abdul ne yace "To ina ne gidanku?" Kallonshi tayi cikin share hawaye tace "Da nisa, ni ba 'yar garin nan bace." Abdul ne ya sake cewa "Kuma kin tabbatar baki san inda zaki je ba?" Cikin kuka tace "Kwana na hud'u a garin nan ina yawo bansan inda zan nufa ba." Abbas ne yace "To amma baki kowa anan ne?" "Bana da." Ta fad'a a tausashe, da mamaki yace "Amma kinsan baki da kowa me yasa kika zo nan?" "Bani ce na zo ba, k'addara ce ta kawo ni nan." Ajiyar zuciya Abbas ya sauke yana tunanin abinyi, ya d'an jima a haka har Ma'arufa ta jawo jakarta tace "Sai anjimanku." Ta fara tafiya da k'yar tana d'yangasa k'afa Abbas yace "Dakata baiwar Allah." Tsayawa tayi ta juyo shi kuma yace "Idan ba damuwa ki zo muje gidana, saina kira dr ya duba ki tunda kin k'i yarda muje asibiti." Shiru tayi tana jin wani farin ciki na shigarta na samun nasara, dan a yanda suka shirya dama shiga gidan ne zai musu wahala, amma tana shiga babu abinda zai tsayar da ita aikin daya kaita kawai zata fara, jin shirun yayi yawa hakan yasa Abdul cewa "Ki zo muje kinji, kar kiji tsoro, Abbanmu mutumin kirki ne, ki d'auka daga yanzu har zuwa lokacin da zaki bar fadarshi zaki kasance cikin aminci ne." Jim ta sake yi alamar tsoro kafin tace "Na yarda zan biku, Allah yasa va zaku cutar dani ba kamar yanda wanda na zo domin shi garin nan ya nemi cutar dani." Tabbas akwai labari mai ban tausayi a cikin rayuwarta, amma kuma ba yanzu ne lokacin da zasu sani ba, dan haka ta taho ta shiga da k'yar kafin suma suka shiga suka tayar, bata fi tafiyar minti biyu ba suka tsaya k'ofar gidan, horn yayi mai gadi ya bud'e mishi k'ofa tare da musu barka da zuwa, suna ratsawa suka shiga Ma'arufa ta saki baki tana kallon gidan, cab'! Ashe dama wannan masarautar ya gina ya shiga shi da iyalinshi? Gaskiya gurguwar nan ta cuce mu da bata bari wannan ya zama ubanmu ba, da wannan tunanin da take taji motar ta tsaya sun fita, fitowa tayi ita ma inda tabi bayansu tana sake k'are ma gidan kallo, kai kasan maganar ma ace an kashe kud'i a wurin b'ata yawun baki ne, dan ko a k'asashen waje ka gida wannan gida dole asan ka tara masu gidan rana, ji tayi kamar zata fad'i a daidai lokacin da ta taka k'afarta a teress d'in falon, ga wani masifaffen sanyi da k'amshi daya daketa, a lokacin suna kan dinning suna cin abinci dan haka suka zarce can, a tak'aice dai ta samu tarba sosai a gurin kowa da kuma sakin fuska banda Abba wanda har yanzu ranshi a b'ace yake, abincin ma ya fito ci ne saboda yaran karsu damu da damuwarshi tunda haka aka saba, nan Ma'arufa ta zauna aka yi serving d'in ta ita ma tana ji kamar tace wayyo ta wayyo kanta, abincin dare d'aya amma kai kace wata walima ce tasa aka shirya, nan suka ci abinci aka gama sai cewa tayi zata tafi, duk yanda suka so da ita ta bari a kira likita ta k'i, aka suka hak'ura Ammie tace bai kamata ta tafi ba tunda dare yayi kuma tace bata san kowa ba, a haka Ma'arufa ta samu yanda take so ma'ana masauki a gidan. D'aki ne dake k'asa kuma babu tazara tsakaninshi dana Sameera, babu abinda babu a ciki dan Sameera ce ke kula da shi saboda saukar bak'i idan sun zo daga basraba, duk da wani lokaci idan ta b'atawa Abbas rai yana cewa kishiya zai mata kuma ya sakata a d'akin, amma sai tace ai babu mai k'arar kwanan da zata yarda ta shigo mata gida, ko shi saita k'ona shi da ranshi idan yayi wasa, to fa anan Ma'arufa ta sauka ta samu tayi wanka ta canza kaya, kafin ta kwanta Ammie ta turo Raudat da magani wai ta shafa a k'afar ta ko taji dama dama, har Raudat zata fita Ma'arufa tace "Ya sunanki?" Juyowa tayi da fara'a tace "Raudat." Murmushi ta mata kafin tace "Zo zauna muyi hira lil sis." Dawowa tayi ta zauna tana kallonta ita kuma tace "Ina Ummynku take ne? Ko kuma mahaifiyarku ta rasu kamar ni? Dan na fahimci wacce kuke kira da Ammie kamar granny d'in ku ce ko?" Bud'ar bakin Raudat sai cewa tayi "... *Sub'ul da baka.* 👏 12/06/2020 à 11:49 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _9_ Tunda Allah ya halliceta take zaune shekara goma sha bakwai a matsayin matarsa bata tab'a sanin cewa baya k'aunar ta ba irin yau, to mana baya k'aunar ta, dan rashin imanin daya darza mata ko dabba kayiwa haka kasan sai dai a d'auki gawarta, tabbas tasan akwai fyad'e a duniya, domin kuwa ita ta hanyar fyad'en ma ya rabata da nata budurcin, amma sanin azabar dake tattare da haka bata sani ba kam sai yau, babu inda bata jin yana mata zafi a jikinta, kama daga labb'anta wanda har cizasu yake tsabar mugunta zuwa kan k'irjin ta daya dinga lindasu kamar yana wankin kayan da suka shekara ba wanki, k'asanta kam ko magana ma ba ayi, duk da uwa ce ita ta haihu amma gyara da kular da take bawa wurin yasa yake zam-zam, to a yau dai kam ta tabbatar ya gama wangaleta ta yanda ko d'inketa akayi ba zata sake birgeshi ba bare ya moreta, cikin wannan hali da take taji ya kasheta da wani tattausan mari wanda ita a wurinta wata azabar ce ya biyota da ita, mik'ewa yayi ya fad'a ban d'akin ta ya tsarkake kanshi, yana fitowa ma jakar daya jefar ya d'auka ya d'ora akan gado ya bud'e ya d'auki kayanshi ya saka, sai lokacin ya kunna hasken d'akin ya kalleta. Sam baiyi dariya ba saboda baya so ta samu damar sauke mishi tijara, amma yasan yau kam mai rabasu sai Allah, ko bata zage shi ba saita dake shi, har zuciyarshi yasan tana buk'atar taimako, amma danya d'an fara bata tsoro idan yace tayi sau d'aya ba sai ya maimaita ba yasa ya k'are mata kallo ya fita a d'akin, tana ganin haka ta tattara k'arfinta ta mik'e zaune da k'yar, kallon kanta tayi ta madubin dake gefenta tace "Ni zai yi wa haka? Lallai ma mutumin nan." Misalin *09:00* na dare suna zaune dukansu kan dinning table, sanye take da doguwar rigar material mai kyau da tsada bleue light da d'an kwalinta, babu komai a fuskarta data shafa idan ka cire mai da lips a bakinta, tana hango Ammie zaune ta sake sangarta tafiyarta cikin shagwab'a ta k'arasa ta rumgumeta ta baya ta fashe da kukan sangarta, da sauri Ammie ta fara tambayarta "Auta ta lafiya? Waya tab'a min ke?" Abbas da tunda ta fito yake kallonta, maganar gaskiya kallo d'aya ya mata ya ga har tayi wata ramar k'arfi da yaji, hatta tafiyarta ma ta kasa daidaituwa da kyau duk jikinta ya saki, wani haushi ne ya tokare masa mak'oshi yaji kamar ya mareta, shin bata lura da bak'uwar dake wurin bane? Idan ma bata ganta ba ai tasan Abdul na wurin yaron dake shirin zama sirikinta, kasa amsawa tayi yayin da yaran duk suka k'ura mata ido har da Ma'arufa dake mamakin karuwanci Sameera, Ammie ce ta gyara zamanta kan kujerar da nufin zaunar da Sameera kan k'afafun ta, amma suna had'a ido da Abba taga kallon da yake ma Sameera tasan duk yanda za ayi zai iya d'aukar wuk'a yace zai gagara mata, dan haka ta mik'e tsaye tace "Auta zo muje d'aki na ki fad'a min meya sameki, naga duk kin canza kamar ba ke ba." Hannunta Ammie ta kama zasu fice sai idonta ya sauka kan bak'uwar su, yanzun ma kamar ganin ta da ita na farko sai taji gabanta ya fad'i tare da jin haushin yarinyar, wani tunani ne ya d'arsu a zuciyarta take a wurin, shin idan fa k'addara tasa yarinyar ta aurar mata miji? Kanta ta bawa amsa ta hanyar fad'in "Ai kuwa babu abinda zai hanaki k'ona gidan nan kamar yanda kike fad'a masa." Da haka suka tafi part d'in su Ammie suka zauna falo, cikin rarrashi Ammie tace "Auta fad'a min meya miki?" Turo baki tayi gaba ta kwantar da kanta saman k'afafun Ammie tayi shiru, cire mata d'an kwalin tayi ta fara shafar kanta data ji shi a jik'e, take ta fahimci komai, dama ba kunya ce tsakaninsu ba dan haka Ammie tace "Auta halan hukuntaki yayi saboda baki taho tare da mu ba?" D'agowa tayi ido taf da hawaye kamar zata fashe da kuka tace "Ammie hukuncin ma mai tsanani, wallahi bai tab'a min irin shi ba sai yau, bansan a ina ya koyi wannan muguntar ba, ni gaskiya Ammie daga yanzu d'akin ki zan kwana har saiya bani hak'uri." Kwantar da kanta tayi tana daddab'ata b'angare d'aya tana toshe baki tana dariya, labari ta fara bawa Ammie yanda sukayi da matar waziri, dariya kawai Ammie take tana godewa Allah da abun ya tsaya iya mari kawai, suna haka sai ga Abbas ya shigo tak'im tak'im kamar wanda aka bawa sarauta, Ammie na ganinshi ta had'e rai tace "Kai kuma malam lafiya? Meya kawoka wajenta?" Saida ya harari Sameera yace " Ni ba wurinta na zo ba." Zaune yayi kan kujerar dake fuskantarsu ya kalli Sameera dake wurga masa harara yace "Ke tashi ki bamu wuri zamuyi magana da uwa ta." Sake mak'alk'ale Ammie tayi tace "Ba zan je ko ina ba, ka fad'i duk abinda zaka fad'a ina gaban uwata." Murtuke fuska ya sake yi, matsalarshi da ita daman kai tsaye zai bata umarni tace ita ba haka ba, kafeta yayi da ido kawai hakan yasa Ammie kallonta tace "Yarinyata, shiga d'aki na ki kwanta abinki gani nan zuwa yanzu, idan kin shiga ki duba a drower akwai kayan dad'i ki d'auka kinji." Mik'ewa tayi a kasalance ta wuce ko d'an kwalin nata bata d'auka ba, da kallo ya bita kafin ya kalli Ammie wacce tace "To ina jinka, lafiya da zaka wani katsewa yata jin dad'in ta?" Mik'ewa yayi yace "Ba komai, dama zan d'an fita." Kafin tayi magana taga ya sa kai ya nufi d'akin nata kuma, girgiza kai tayi tace "Kaji da munafurcinka, da nace wurinta ka zo ai cewa kayi a'a." Sameera na sunkuye zata d'auki chocolat taji saukar mari a mazaunanta, da sauri ta d'ago ta dafe kayanta tana fad'in "Washhhh." Tana ganin yanayin shi sai kuma tayi shiru, cikin muryar shagwab'a tace "Dan Allah Abban Ameer ka daina wahalar dani haka, ya kamata fa ace yanzu na wuce ajin shan wahalarka, wacce na sha ma a baya lokacin da nake maka bauta ta isa haka." Yana kallon k'aramin bakin har saida ta dasa aya sai kawai ya had'ata da bango ya had'e bakinsu, wani bala'in kiss ne yake mata mai matuk'ar zafi kamar zai cire mata labb'a, tuni idonta suka kawo ruwa ta rufe ido wasu hawaye masu zafi sirara suka shiga fitowa suna bin kumcinta, a gefen fuskarshi ne ya ji alamar lema hakan yasa ya tsaya yana kallonta, cikin wata irin murya ba tare daya matsa daga cikin jikinta ba tace "Sam ki dinga jin magana ta mana, bana so muna irin haka dake dan mun girma yanzu, ki ce zaki dinga ji duk abinda na fad'a miki, ni kuma ba zan sake bari ki zubar da hawaye ta dalili na ba." Bud'a ido tayi cikin shashek'a tace "Zan dinga jin maganarka indai kayi alk'awarin ba zaka sake min irin muguntar nan ba ta yau?" Yanda tayi maganar saiya k'ayatarda shi, bud'e mata hannayenshi yayi alamar ta taho, sake fashewa tayi da kukan da bata san dalilinshi ba ta fad'a cikin lafiyayyen k'irjin shi, matseta yayi sosai yace "Na miki alk'awarin ba zan sake ba indai nima zaki dinga jin duk abinda zan fad'a miki." Cikin shashek'ar kuka tace "I promise u, please forgive me." Cikin shafar tattausan bayanta yace "I forgive u my Meerata, i really love u." Sake k'amk'ame shi tayi a haka suka fito falon tare, Ammie na ganinsu rumgume da juna sai ita taji kunya, dama kuma ba sabon abu bane a wurinta, kullum suka samu matsala saita tsaya bayan Sameera ko tasan ita ce bata da gaskiya, ba jimawa kuma sai ka gansu a had'e a jone. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Abbakar ne ya samu Saleem a d'akin shi yana waya da Fadila kamar sun jima da fahimtar junansu, yana ganin shigowarshi ya datse kiran yana fad'in "Yah Abbakar, kaine yanzu?" A hankali ya k'araso cikin jan k'afar shi ya tsaya kusa da shi yana kallonshi yace "Saleem baka kwanta ba har yanzu?" Murmushi yayi yace "Ban kwanta ba yah, amma kai ma ya akayi baka kwanta ba har yanzu?" Shima murmushi yayi yace "Ina ta tunaninka ne Saleem." Da mamaki yace "Tunani na kuma yah? Akan me? Ko dai tunanin Zeenat?" Girgiza kai yayi yace "Tunaninka nake Saleem, tsoro kake bani, ina gudun kar kaje kayi abinda zai saka mu cikin matsala, shiyasa na gagara bacci har na zo na sameka, kwanan nan kana wayon fita kuma baka zama sosai a shago, sannan kashe kud'in ka ya k'aruda kaso goma, me kake yi da kud'i Saleem? Ina kake zuwa idan ka bar shago?" Cike da nuna alamun rashin gaskiya ya fara shafar kai yana fad'in "Yah ba komai fa, ka yarda dani mana, ni fa yanzu ba k'aramin yaro bane, nasan abindake daidai da wanda ba daidai ba, so calm down bros." Ajiyar zuciya ya sauke yace "Saleem kai ba yaro bane, amma dai kasan ina gaba da kai ko? Please Saleem ka fad'a min idan akwai wani abinda ke damunka, na maka alk'awari insha Allah zan taimaka wajen solven matsalarka, amma bana so kaje kayi abinda ya sab'awa shari'a da ma al'ada da mutuntaka ta d'an adam." Shiru Saleem yayi baice komai ba, jin ba zaiyi magana ba yasa Abbakar cewa "Saleem idan kana da matsalar sha'awa ne ka fad'a min sai mu maka aure, amma karka jefa kanka a harkar neman mata, mummunan zane ne da zaka yiwa kanka na har abada." Cike da k'aguwa ya kalleshi yace "Yah ba komai fa, dan Allah kaje ka kwanta, ba zan tab'a neman mata ba kai ka sani." Cikin sanyin jiki ya juya ya bar d'akin inda Saleem yace "Har na fara jin k'amshin yanda zan kuntatawa rayuwarsu zaka zo min da wata magana, yanzu kana komawa d'akin ka hoton matsiyaciyar yarinyar nan zaka d'auka ka fara kallo har gari ya waye maka." ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Gari na wayewa yau yan matan suka shirya driver ya kaisu school dubo result d'in, suna zuwa kuma basu sha wahala ba suka samu sakamokonsu mai kyau suka juyo cike da murna, kai tsaye gida suka sake dawowa, suna zuwa da farin ciki kowace ta nuna nata, gaskiya ne Raihan tafi k'ok'ari sai Fadila sai kuma Ma'awa, hakan yasa Bashir da Naseer suka dinga yabawa Raihan har kowane yayi alk'awarin kawo mata kyauta, Abbas kuma su Fadila ya dinga yabawa wanda yasa Fadila jin kawai yana yaba musu ne saboda iyayensu basu yaba musu ba, shima cewa yayi zai bawa kowace kyauta, suna tsaka da raharsu Harira ta fito cikin kwalliyarta kamar yanda ta saba yanzu ta kawowa Ameer takalminshi, saida ta durk'usa har k'asa ta saka mishi takalmin kafin ta mik'e ta juya tana jijjiga, duk da Sameera ta ga hakan amma saita barshi a matsayin zawarci tana neman mijin aure ne, kuma tasan babu abinda mijinta zaiyi da Harira, dan haka bata damu ba, nan Abbas yace yaran su shirya sai su fara tafiya basraba, nan da sati biyu idan aka gama bikin Husna sai a tafi tare da su kan amarya daga nan zasu iya yin hutun su a can, sunyi farin ciki sosai saboda zasu fita wata k'asar da ba tasu ba. Da dare kam su Bashir sun cika alk'awari ta hanyar kawo musu kyaututtukansu, sai dai Abbas ne ya gwangwajesu da manyan wayoyi yan zamani duk iri d'aya, sunyi godiya sosai tare da binshi da addu'a kafin daga bisani kowa ya nemi gado ya kwanta, Sameera da Abbas ma har sun kwanta ya tuna sam rabon da yaga bak'uwar nan tunda rana, dan duk hayaniyar nan da aka dinga yi tana d'akin ta, dan haka ya fito dan dubata, yau ma k'wank'wasa k'ofar yayi ta bud'e, sai dai yau doguwar riga ce a jikinta ta bacci, tambayarta kawai yayi ya k'afar ta ta amsa da sauk'i ya mata saida safe ya koma, Sameera kuma yana zuwa ta fara mishi mita akan yarinyar nan ita fa bata son ganinta, ya fad'a mata yana so ta samu sauk'i ne saita fad'a musu gidansu ya kaita, amma tace me zai hana ya tambayeta tun yanzu saiya kaita can tayi jinyar? Da dai yaga yana tarota tana zillewa sai kawai yace ina alk'awarin data d'aukar masa jiya jiya? Hak'uri ta bashi tace to yayi hak'uri ta daina kuma zata zuba mishi ido har lokacin daya sallameta. *Bayan kwana biyu*... 12/06/2020 à 15:19 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _15_ Kai tsaye dama yake shiga d'akin Hajia, sallama kawai yayi ya tura k'ofar ya shiga, zaune ya same ta kan gado cikin doguwar yellown riga ta bacci, saida ya ja kujera ta gaban madubinta ya zauna ya kalleta, ita ma shi take kallo tana murmushi kafin tace "Shalele na ka ci abincin?" A dak'ile ya amsa da "Na ci." Cike da kulawa tace "Ina fatan dai baka tare da gajiya ko?" Saida ya sake b'ata rai yace "A'a." Murmushi tayi saboda yanda ya turo baki saita tuna lokacin yana k'arami, mik'a mishi hannunta tayi alamar ya taso, bata hannun yayi ya taso ya zauna kusa da ita ta fara shafar sumar kanshi, a ranta tana ayyana ai dole ma ta so shi, dan kaf cikin yaran babu wanda suka d'auko kalarta kamar shi da d'an uwanshi, hatta gashin kansu ya murd'e yake, dogayen hanci har baka da k'aramin baki jawur da shi, kurmin ido kuma manyan ido masha Allah, sannan gasu zabga zabga wajen tsayi wanda nan kuma kakansu ne sukayi Suley, tana kallonshi tace "Shalele ina fatan dai zab'in dana maka yayi maka ko?" Kallonta yayi da mamaki, wato ta kira shi ne dan taji idan zab'in ya birgeshi, idan har yace bai mishi ba yasan dole zata canza mishi kuma cikin dubara, ganin kallon da yake mata yasa tayi murmushi tace "Kasan wani abu shalele? Ina matuk'ar k'aunar ka a zuciyata, kaine jin dad'i na da rayuwata, na zab'ar maka Umaima ne saboda kaga tafi sauran yan matan wayewa da ilimi, bata da kwaramniya da shiga abinda bai shafeta ba, sannan kaga tana koyon aiki a inda kaima kake aiki, shiyasa na maka wannan zab'in." Shi dama baida matsala da zab'in data mishi, matsalar shi kawai yan uwanshi dake cikin damuwa saboda zab'in nata, dan haka yace "Hajia, ni banda matsala da zab'in da kika min, kin sani nima ina sonki kuma ina son farin cikinki, saidai Hajia 'yan uwa na ba duka ne suka gamsu da zab'in nan ba, idan zai yiwu dan Allah ki bar kowa ya zab'i wacce yake so." Wata hamshak'iyar dariya tayi tace "To meya shafeka da su? Ai ka barsu kawai babu abinda zai faru, duk wanda aka kaiwa macen d'akin shi ba zai fasa kulata ba." Cikin butsuwa yace "Hajiata, aure fa rayuwa ta din-din-din, ya kuke tunanin zasuyi farin ciki idan basa son junansu? Wallahi dukansu zasuji basu da maraba da marasa 'yanci, Hajia dubeki mana ke da Alhaji, a shekarun nan da kuka d'auka tare kina ganin da babu soyayyar junanku a zuk'atanku da zaku iya zama da juna ne? Ko da kun zauna Hajia dole d'aya daga ciki yana jin an takura shi, wannan rayuwar ce bana so yan uwana suyi, Hajia Junaid yana da wacce yake so, wacce yasa mukayi doguwar tafiya dominta, haka ita ma Hamna tana da burin da take so ta cimma, lokacin auren da kika saka yayi daidai da lokacin daya kamata ta fara zuwa koyon darasin zanen ta, yanzu haka kuka na barota tanayi saboda tana ganin kamar an ruguza mata burinta ne, shi kanshi Junaid d'in yana can kukan ne kawai baiyi ba saboda shi namiji ne ya fita dauriya da juriya, dan Allah Hajia ki taimaka ki musu wannan alfarma." A hankalce ta kalleshi tace "To yanzu shalele sun turoka ne ka samar musu abinda suke so?" Murmushi yayi yace "Hajia ban isa su turo ni ba? Na d'auka yanzu kika gama fad'in nine rayuwarki, hakan da suka bai isa yasa su turo ni ba? Sannan ni babu wanda ya turo ni, na fahimci damuwar kowane ne kuma nake rok'a musu alfarma a wurinki, idan kuma ba zan samu ba saina hak'ura, amma dai abun zai tsaya min a zuciyata ace na kasa samun wannan yar alfarmar a gurin kakata da nake da yak'inin babu mafi soyuwa a zuciyarta sama da ni." Shiru tayi ta zurfafa tunani akan buk'atar shalelen ta, ya zatayi Allah ya d'ora mata k'aunar shi, shi kuma jin shirun yasa ya mik'e yace "Saida safe Hajia." Tana kallo yake tafiya harya kusa kaiwa bakin k'ofa, da sauri tace "Shalele na." Cak ya tsaya tare da juyowa ya kalleta, da murmushi a fuskarta tace "Na amince da buk'atar ka saboda jin dad'in ka, ka fad'awa Junaid zanyi magana da iyayenshi suje su nemo mishi auren yarinyar, amma karku d'auka zata samu karb'uwa a zuciya ta dan karuwa ce ita, sai kuma Hamna, ita ma ka fad'a mata zata iya tafiya duk inda take so indai ba zai kai ga fita k'asar waje ba, amma kuma ya zama dole ta zauna ta halarci bikin nan, dan yer uwarta ma na buk'atar ta a kusa da ita, idan sun amince da hakan to shikenan." Dariya yayi sosai ta nuna tsantsar farin cikinshi, da sauri ya zo gabanta ya durk'usa ya kamo hannunta ya sumbata yace "Allah ya bar min ke Hajia ta, nagode sosai da wannan alfarmar." Shafa kanshi tayi da hannu d'aya ta tallabo hab'arshi ta kalli farin cikin dake kan fuskarshi tace " *Amar*." K'ura mata ido yayi dan bai cika jin sunanshi a bakinta ba, d'orawa tayi da "Ka ci gaba da farin ciki irin haka ko da bayan raina ne, wannan shine burina a kan ka, kuma ina fatan Umaima ta zamo macen da zata dinga saka ka farin ciki irin wannan, in tayi haka zata zama suruka ta farko data fara shiga zuciyata saboda kyautatawa, zan so ta, zan k'aunace, zan faranta mata rai, duniya zata mata dad'i, zan so duk abinda ya fito daga cikinta, suma 'ya'yanku zan so duk abinda zai fito daga garesu, kaji ko?" Murmushi ya mata sosai hakan yasa ta kama dogon hancinshi taja tana fad'in "Ka tashi kaje ka kwanta dare yayi, saida safe." Da haka ya baro mata d'akin, bai bi takan d'akin su Ummy ba dan yasan mahaifinsu na nan, a inda ya bar Hamna ya same ta tayi shiru, yana mata albishir taji dad'i, amma daya fad'a mata dole zata kasance a duk wata sabga sai kuma ta marairaice tace "Amma yah Amar ai kamar ba'a rabu da bukar bane aka haifi Abu." Dariya yayi yace "To yanda zamuyi shine, bara na samu Hajia na fad'a mata kin amince da auren ma kawai." Da gudu ta nufi falon tana fad'in "A'a yah Amar ba sai munyi haka da kai ba." A gurin Junaid ma farin ciki ba'a magana, Jibril ya tayashi murna sosai inda Ammar yayi gum yana kallonsu, da wannan kawai suka samu suka kwanta da huta gajiya. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Ko da Zeituna ta shiga gidan yau ma babu wannan hantarar da kyara, abun mamaki ne shine wanka da Jumma tace tayi saita kwanta dan taji dad'i, haka ta shiga wanka amma bata jima ba ta fito, ta zo aje bokitin hannunta ne ta bukkar kawu Mamu taji suna hira a harshen fulatanci, kawu Mamu taji yace "Ki dinga matsa mata fa tana wanka akai akai, dan ni dai ba zan iya fitar da wasu kud'i ba dan gyaran jikinta, shi kuma Alhajin yace baya son k'azanta da tsami." Jumma ce tace "To yanzu ma ba a gabanka ba nace taje tayi wankan ba? Ni wallahi gar yanzu ina d'an d'ard'ar da lamarin ne, bana son mu shiga bakin duniya, ina gudun azo mutumin nan kashe ta ma zaiyi." Cikin fad'a kawu Mamu yace "Ke wai wace irin jahila ce? Na fad'a miki ba kasheta zaiyi ba, buk'atar shi kawai yace zai biya ta duburarta fa saboda akwai aikin da yake so ya cimma, kullum ina gaya miki amma kina wane baud'ewa kamar ke ce za ayi abin da ita." Shiru dai Jumma tayi dan bata iya masifar, wannan batu da Zeituna taji shine yasa taji k'afafun ta na rawa jiri na fizgarta, cikin wani mawuyacin hali ta kai kanta bukkarsu, zaune tayi a k'asa inda ta shinfid'a tsohon hijabinta a kai, kasa fahimtar halin da take ciki tayi tsabar rud'un data shiga, tunda ta d'ora idonta wuri d'aya ta kasa d'aukewa, hakan yasa hawaye bin fuskarta wani bayan wani, tambayoyi ne jere reras take wa kanta kuma ta kasa samun amsarsu, kawunta karuwa yake son mayar da ita? Karuwar ma wacce za'a dinga mu'amula da ita ta bayanta? Nawa ya karb'a domin wannan lalatattar harkar? Wanene mutumin? Meyasa sai ni da ban tab'a iskanci ba zai zab'a? Me nayi kawu Mamu har haka da k'iyayyarshi tayi tsamari a kaina? Ya Allah gani gareka! Allah ka dubi halin da nake ciki ka kawo min d'auki? Domin kuwa da nayi wannan rayuwar da yake son jefa ni har gwara na mutu ace bana raye, tana gama wannan tunanin kuma saita fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, yanda taga safe haka taga wannan dare bata rintsa ba tana sak'ada warwara, ta rasa mafita akan yanda zatayi, da wannan har ta wayi gari tayi abinda ya sawak'ata nufi wajen aikinta. *Gaga's family* Kamar kullum dai Hajia na zaune kan kujerar data saba zama, inda yara da ma wasu daga cikin iyayen ke zaune gefe sai maganganu k'asa k'asa, ko karyawa ba ayi ba bare kowa ya kama gabansa, Hamna da Amna da Jamila ce suka fito tare cikin shirinsu na uniforme (tenue) d'in makaranta, dukansu da Hijabi amma banda Hamna da siririn d'an kwali ne kawai ta d'ora, kayan nasu komai ido d'aya ne ita da Amna hijabi kawai ya banbanta su, yanda suka saba haka suka gaishe da Hajia da kuma Sa'ada da lieutenant dake kusa, ganin Amna da Hamna zasu fita yasa Sa'ada cewa "Yan biyu na tafiya zakuyi ko karyawa bakuyi ba?" Cikin taushin murya Amna tace "Ummy kinsan yanzu ana kusan jarabawa ne, wallahi ana yawan yi mana jarabawar bazata a classe." Lieutenant ne yace "To akwai kud'i aljihunku ko?" Hamna ta amsa da "Akwai Abba, sai mun dawo." Har sun juya zasu fita suka ji muryar Hajia tace "Ke ai kinji sak'o na ko?" Juyowa sukayi sai Hamna da tace "Eh Hajia, na ji." Cike da gadara tace "Da kyau, tunda kin zab'i zama yar fashion amadadin zama matar aure sai kije kiyi, nasan dai duk tsiyar ba zata wuce uwarki ce ke zugaki ba, kuma ni nafi k'arfin ta wallahi, dan haka babu inda zaki ji har sai an gama bikin nan." Shiru Hamna tayi tana kallon k'asa tana gunguni inda maganar kuma ta kashe Amna, ita kullum Hajia saita zagar mana uwa ta d'ora mata laifin da bata ji ba bata gani ba, a wulak'ance tace "Ku b'ace min da gani." Juyawa sukayi suka fita a hanyarsu ta fita kuma suka had'u dasu Amar zasu shigo falon, gaisawa sukayi cikin mutumci kafin Hamna ta kalli Junaid sai taji kunyarshi ta kamata kar yayi tunanin ta k'i shine, shi kuma murmushi ya mata na suna cikin farin ciki kawai, fita sukayi Hamna na mamakin ko ina boss d'in yau, suna nufa inda zasu d'auki motonsu suka hangeshi yana waya. Gabansu ne duka ya fad'i wanda a wajen Amna sabon al'amari ne daya fara zuwar mata yau, masha Allah cewar ta a zuciyarta, hak'ik'a k'ananan kaya na bala'in mishi kyau, kamar kullum kuma takalminshi k'afa ciki ne inda ya d'aure wuyanshi da cravete (nikctie) kai ka rantse *jan kunne* ne idan ba magana yayi ba, cikin tsoro Amna ke tafiya ta sanda kanta k'asa dan bata so su had'a ido, inda Hamna dake rik'e da makullin motanta take gaba sai kace idan sunje za tayi wata tsiyar, kasancewar ba tsaye yake wuri d'aya ba yana d'an kai da kawowa yasa shi d'an zaunawa kan motan nasu, suna isa suka tsaya inda Hamna ta d'an rik'e kan mota tana nesa da shi tace "Bossss..." Da sauri ta kama bakinta dan tasan ko da gudu ya bita zai tarar da ita, shi kuma yana d'ago idonshi akan Amna ya sauke wacce ta tsaya daga gabanshi nesa da shi, ganin ta k'i yarda su had'a ido yasa shi k'arewa fuskarta kallo, saida ya gama kallonta tas ya d'an karkata idonta ya kalli Hamna dake bayanshi tsaye ta madubin moton, kowace shigar da tayi ta dace da ita, Amna kuma duk da tana jikin hijabi amma kasan ita ma yar duma-duma ce kamar 'yar uwarta, hak'ik'a Hamna tafi haske, amma baisan dalilin da yasa yau kuma yanzu daya kalli Amna ba sai yaga duhun nata ma mai kyau ne, sannan sai yaga tafi mishi kyau akan ita Hamna, a hankali ya mik'e daga kan moton ya juyo da dubansa kan ta, babu alamar wasa bare raha, kallon da yake yamutsa mata lissafi ya mata cikin muryarshi dake tayar mata da hankali yace "Baki iya gaisuwa?" Saida ta turo baki gaba tana zuntoshi tace "Ina kwana." Sake kallon surarta yayi sai yaji haka kawai ranshi bai mishi dad'i ba ganin kayan sun kama jikinta, duk da ba sosai bane suka matseta amma dayake anfitar da gurbin komai yasa komai d'in fitowa, masha Allah faffad'an k'ugunta ya kalla ta k'asan ido, da sauri ya d'ago cikin tsawa yace "Dan ubanki maza koma ki sanyo hijabi, kuma wallahi kika k'ara bari na ganki babu hijabi sai ci uwaki gidan nan." Juyawa tayi ta sa kukan shagwab'a harda bubbuga k'afafu take tana tafiya kamar zatayi gudu, "Shegiya!" Ya fad'a a ranshi a zahiri kuma yanda k'ugunta ke kad'awa yasa yace "Kankana." Dole ta tsaya ta juyo dan kiran sunan da yayi cikin wani yanayi ne dake nuna kifa kiyayeni, k'ara d'aure fuska yayi yace "Ba zaki iya tafiya a hankali bane har sai kin tashi hankalin wad'anda ke kwance k'asa?" *Maganar nan da biyu, sai dai bangane manufarta ba* Daina bubbuga k'afafun tayi amma bata daina saurin ba da kukan, saida ya ga shigarta ya d'an juyo a hankali, Amna na ganin zai juyo kanta tayi saurin cewa "Yah Ammar ina kwana." A hankali ya taka kusanta yana kallonta da mayatattun idonshi da lokaci d'aya ba zaka iya fahimtar manufar kallonshi, saida yaga ya k'ureta kad'ai ya tsaya kamar zai ci tuwo a saman kanta, Amna da ke jin kamar ta sako fitsari jira take taji yace dan ubanki bakiyi abu kaza ba, amma taji shiru gashi babu niyyar ya d'an bata wuri tasha iska, shi kuma baiwar da Allah ya mishi yasa yake iya hango yanayin da take ciki a goshinta, ji tayi yace "Kalle ni." Gudun laifi yasa ta d'ago da sauri ta kalleshi, kamar saukar aradu a kanta taji yace "Tun yaushe kika fara al'adarki?" Wani bazawarin tari ne ya taho mata bata san da zuwanshi, da sauri ta rik'e tarin ta hanyar rufe bakinta gam tana kallonshi, gashi kuma yayi alamar kamar na shi yayi maganar ba, k'asa tayi da idonta ta kasa cewa komai, ji tayi ya sake cewa "Ki tabbatar kafin aurenmu kin shirya fad'a min lokacin da kike farawa, da lokacin da kike gamawa, sannan yaushe kike wankan tsarki?" Yana gama fad'a ta hange shi cikin wannan takon nashi na in sojojin sun motsa a kanshi, baki sake ta maimaita kalmar " *Kafin aurenmu*, kenan ma yana son auren? Anya kuwa zan iya?" Firgigit tayi ta sake kai dubanta hanyar falon Hajia amma tuni har ya shige, yana shiga kuma Hamna ta fito da hijabi sai turo baki take, ko kallonta baiyi ba saboda fad'uwa da yaji gabanshi yayi, kamar yanda ya saba babu sallama babu fara'a ya k'arasa yana kallon kujerar Alhaji amma kuma baya nan, tun kafin ya isa kusan Hajia ya wani d'aga mata hannu irin na inka had'u da mutum a kan hanya kuna kan ababen hawa wato yar hannu, kai tsaye ya sauke hannunshi yace mata "Barka da zama." Ummy da tunda ya shigo dama take takaicin wannan d'abi'a tashi ta rashin sallama hararanshi tayi, wato dai baya jin magana? Yanzun ma so yake saiya ja mata bala'i sannan ya bar gidan, lieutenant ma kallonshi yake wato ita Hajiar ta ma samu barka da zaman? Su kuma ko oho ko? Juyawa yayi ya kalli Ummy yace "Na jiraki ne ko zaki taho a motarki?" Rarraba ido tayi tana tsoron bashi amsa Hajia ta juye kanta, lura da yayi da hakan ne yasa shi juyawa ya kalli Hajia, ganin tana hararenshi tana so taga gudun ruwanshi yasa ya kalleta da kyau yace "Shi kuma wannan hararen me sunanshi?" A hassale Hajia tace "Ubanka, nace ubanka." Mayar da fuskarshi alamun ko in kula yayi yace "To ba gaki ga shi ba." Ya fad'a da nuna mata lieutenant da yake mamakin yanda Hajia ke biyewa lamarin Ammar, nuna shi tayi da yatsa tace "Kai bari kaji magana ta k'arshe, wallahi tallahi in ka sake zuwa gabana da wannan gaisuwar rashin mutumcin taka sai na ci ubanka nan gidan, Ammar ni zaka d'auka mahaukaciya? To wallahi ka kiyaye ni, idan ma k'wank'wanmai ne a kanka ka sani nawa sun dame naka sun shanye, kuma aure ne babu fashi ko zaku mutu sai an d'aura shi." Gyara tsayuwa yayi da kyau yace "To banda abinki Hajia na nuna miki bana son auren ne? Ba dai aure ne ba? To a d'aura, shawara kawai zan baki ki gogar da jikarki dubarun zama da ni, dan inba haka ba wallahi zata sake dawowa gabanki ta tare, aure kam ai ni shirye nake da a d'aura shi ko yau ne, lafiya ta k'alau wallahi ina da ingancin da zan iya tafiyar da mace hud'u ma a dare d'aya, ci da sha da sutura bata da matsalarsu saboda duk iyayenta masu kud'i ne, wannan hakk'in ne kawai ba zanyi wasa dashi ba wajen saukewa." Tsayawa yayi kamar an taka masa birki ya d'an juya ya kalli su Amar dake zaune suna kallon ikon Allah, d'orawa yayi da "Hajia kin manta da wani abu, tun ranar da aka haifeni k'wank'wanmanki suka dawo kaina." Ciro gilashin shi yayi gaban aljihun rigarshi ya manna a idonshi ya juya, lieutenant ne ya mik'e ya fizgo rigarshi, hannu ya d'aga da niyyar marinshi sai Hajia ta dakatar da shi ta hanyar fad'in "Barshi." Kallon Hajia yayi ya saki rigar Ammar shi kuma saida ya gyara rigar ya wuce yana fad'in "Babu abinda dukanku zaiyi min da baiyi min shi ba a baya." Hajia kuma kallon Sa'ada tayi wacce ita fa take ganin duk rashin mutumcin da Ammar keyi ita ke d'aure mishi gindi, k'wafa tayi ta harareta ta wuce d'akin ta da tunanin koyawa uwar tashi hankali sai taga ta tsiyarshi ai. Alhaji na d'an tattaki a gaba d'aya gidan harya isa bayan gidan, tsayawa yayi ganin Zeituna wacce abun duniya ya isheta tana kuka, girgiza kai yayi dan yasan matsalar ba zata wuce Hajiar shi ce ta mata wulak'ancin data saba, takawa ya fara yi da niyyar zuwa ya bata hak'uri, sai kuma ga Iya ta fito daga d'aya hanyar dake sadaka da bayan gidan da mamakin ganin Zeituna tana fad'in "Subhanallahi! Zeituna dama nan kika zo kika zauna? Ina can ina nemanki ki ka ma min d'auke kujerun wurin nan mu share wurin, amma kuma..." Shiru tayi ganin Zeituna na kuka, da sauri ta k'araso Alhaji kuma ya tsaya, kusanta ta zauna ta dafata tace "Zeituna lafiya? Me akai miki kike kuka?" D'agowa Zeituna tayi ta kalleta cikin goge hawaye tace "Iya, kamar mahaifiya na d'auke ki, bayan iyaye na babu wanda ke nuna min kulawa kamar ke, Iya wani abu yana damuwa na sosai a zuciyata, na b'oye nayi addua'r Allah ya cire min amma har yanzu babu sauk'i, yanzu gashi wata masifar na neman kunno min kai, Iya zan fad'a miki matsala ta watak'ila na samu sauk'in abinda ke damuna, amma Iya dan Allah ya zama sirri tsakani na dake, kuma bana so kiga wautata ko shirme na da haukana, shawara kawai nake so ki bani Iya." Ajiyar zuciya Iya ta sauke cike da dattako ta dafa kafad'ar ta tace "Nima kamar 'ya na d'auke ki Zeituna, ki fad'a min matsalarki insha Allah zamu samu mafita, kuma zan fahimce ki da yardar Allah, sannan babu wanda zaiji maganar nan." Gyara zama Zeituna tayi ta fuskanci Iya da kyau ta kalleta da idon basira tace "... _Duk wanda yasan zaiyi comment zai iya kasancewa grp d'ina ta hanyar neman wannan lambar *88-35-50-01*, ko kuma wannan *+213-65-81-91-316*, ko kuma wannan *99-32-99-10*, kuji da kyau wanda yasan zaiyi comment kawai._👏 16/06/2020 à 13:21 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _17_ Tunda Junaid ya samu labarin gobe za'a je neman auren Maryama hankalinshi ya tashi , sam bai d'auka abin zai zo da wuri haka ba, duk da shi ba matse yake da yayi aure ba, amma tunda wacce zata aurar dashi d'in ta amince dole ya gaggauta, kiran Iklima yayi yace ta dubi Allah ta dubi annabi ta had'a shi da Maryama yana so suyi magana mai mahimmanci, magiyar da yayi mata tasa tace ba damuwa ya zo gida suna nan, saida ya d'auki wanka cikin k'ananan kaya yayi kyau sosai sannan ya fito, har zai shiga motar shi saiga Jibril ya shigo, takowa yayi wajenshi yana fad'in "Yawwa d'an uwa, gwara da Allah ya kawo ka, wani taimako zaka min dan Allah." Cikin sakin fuska Jibril yace "To wane irin taimako kuma malam?" Tsaye yayi ya bashi hannu suka gaisa yace "Yanzu haka wajen Maryma na nufa, Iklima ta min alk'awarin ganinta idan naje, sai dai Maryama tana da taurin kai sosai, ina so ne muje ka rakani dan Allah wala'allah ko in ta ganka zata saurare ni, dan ya kamata ace yau ta koma gida saboda gobe su Abba zasu je garinsu nema min aurenta." Ido Jibril ya fiddo yace "Toh, da wuri haka? Amma ni..." Katse shi yayi da cewa "Amma kai me? Dan Allah d'an uwa karka ce a'a, ka taimaka min muje, in kuma ba zaka je ba saina je na d'auko Ammar duk inda yake." K'ara zaro ido yayi yace "Ammar fa kace? Kai yanzu zaka yarda kaje wurin matar da kake son aura da Ammar? Lallai." Dariya Junaid yayi yace "To miye a ciki? Shi ba mutum bane?" "Mutum ne, amma kasan danya d'udd'ura mata ashar k'aramin aikishi ne ko." Kafin Junaid yace wani abu Jibril yace "Jirani kawai na zo mu tafi, amma sai nayi wanka nima." Cikin gidan ya nufa Junaid na fad'in "Sai ka ce wanda zaije neman kasuwa, ko ka manta kai kana da matarka?" Bai wani jima sosai ba ya shirya ya fito ya shiga b'angaren iyayen ya gaishe su sannan ya fito, ya fito kenan a farfajiyar suka had'e da Jamila zata shiga falon, k'asa tayi da kanta tace "Ina wuni." Cikin dakakkiyar murya ya amsa da "Lafiya lau, me kike a waje?" Sororo ta kalleshi a ranta tace "Tofa! Wai kowa daya samu dama saiya dama tsiyarshi." Saida ta kalli k'wayar idonshi tace "Ba daga waje nake ba, daga bayan gida nake." Baice komai ba yasa kai ya wuce saida ta juyo ta kalleshi, yana samun Junaid suka fita daga gidan suka d'auki hanya sai gidansu Maryama, suna zuwa Iklima ya kira yace gashi waje, sosai Iklima tasha daga da Maryama kafin ta fito daga d'akin suna fad'a, a k'ofar gidan ta samu Huda tare da yara suna wasa, hannunta ta kama da tunanin idan sunje ya ga Huda ba zai mata wannan maganganun nashi ba da ba zasu anfaneta ba, daga cikin kwana inda suka paka mota ta shigo, tana zuwa taja ta tsaya ta jingina a motar a b'angaren da take tunanin babu kowa dan bai tab'a zuwa mata da kowa ba, ta k'ofar da yake tuk'i ya fito ya zagayo wurinta yana doka murmushi da fad'in "Gimbiya sarautar mata, Maryama kina lokaci fa, gani na ma sai kin so." Cike da jan aji tace "Hakan yafi ko? Asha wuya kafin a ganka." Murmushi yayi ya dafa kan Huda yana kallonta yace "Huda ya kike? Ya karatu kuma?" Da murmushi yarinyar ta amsa da "Lafiya lau, ina wuni." "Lafiya lau Huda, ke ba kya baccin rana kenan?" Ya fad'a yana kallon Maryama, shiru Huda tayi dan kallon da Maryama ta mata bata fahimci me yake nufi ba, kallon Maryama yayi yace "Mari magana na zo muyi dake mai mahimmanci, amma kafin nan zan so ku fara gaisawa da d'an uwa na Jibril." K'ofar daya nuna mata yasa tayi saurin tasowa daga jinginar da tayi ta juyo tana kallon k'ofar, bud'e k'ofar Junaid yayi yace "Malam saika fito ko." Zuro k'afa yayi ya fito sannan ya fito da d'aya k'afar yana murmushi da kallon Junaid yace "Ai na d'auka ka manta da ni zakin soyayya." Kai tsaye kuma ya kalli Huda dake kallonshi ita ma tana murmushi, murmushi ya mata yace "Sannu bebbbbbbbbb." Cak ya rasa maganarshi saboda kallonshi da ya kai kan fuskar da duk da akwai canji amma ba zai tab'a mantawa da ita ba har abada, dakan uku uku k'irjin shi ya shiga yi a lokaci d'aya kuma ya ji komai na jikinshi ya tsaya daga gudanar ruwa da jini har zuwa numfashinshi ma neman gagararshi yake so yayi, ba zaka ce yana da rai ba inba dan zufar dake tsatsafowa daga kowace k'ofa ta jikinshi ba. Irin dai yanayin d'aya ne da Maryama ita ma ta shiga, k'uri ta mishi da ido tana kallo ba ko k'yabtawa, zufa da hawaye kam har tsere suke wajen fito mata, mutumin da kullum saita zage shi kafin bacci ya d'auke ta? Mutumin data rabu da iyayenta a dalilinshi? Mutumin da mahaifinta ya rasu ba akan idonta ba a sanadiyarshi? Mutumin da yake da babban kaso na duk zunubin da take aikatawa? Uban 'yarta da kullum take son gani? Wai yau shine a gabanta? Wannan wace irin rana ce? *Fara ko bak'a a gurinta*? Tasan dai a wurin Huda fara ce kam, wannan yanayin da Junaid ya gani a tare da su yasa shi dafa Jibril yace "Ya dai malam? Ko ka santa ne?" Sakaka ya kalli Junaid ya rasa me ma zai fad'a masa, wannan wane irin tashin hankali ne? Maryama ce tayi k'arfin halin kallon Junaid tana shafe zufa tare da hawayen dan kar ya gani tace "Kamar ya ko ya sanni?" Murmushi Junaid yayi yace "A'a ranki shi dad'e ayi hak'uri, ni ba wani abu nake nufi ba, kawai dai naga yayi wani iri ne." Ya k'arashe yana kallon Jibril dake satar kallon Maryama, yana ganin sun kalleshi yayi saurin kallon Huda yana cewa "D'an uwa wannan ce matar ta mu kenan?" Wani kallon mamaki Junaid ya masa dan yanda muryarsa ta fita zaka iya fahimta tashin hankalin dake cikin sautin, ganin Maryama da Junaid duk kallonshi suke kallon daya kasa fahimta gashi duk ya tsargu, dan haka ya sake kallon Huda ya mata murmushi ya zura mata hannu alamar ta taho yana fad'in "Beby ya sunanki?" Zuro mishi hannun tayi tana fad'in "Nurul Huda." Kusa da shi ya tsayar da ita yana kallon kyakyawar fuskarta mai kama data uwarta, gabanshi har yanzu bai daina fad'uwa, ga wani sabon tashin hankali daya ziyarce shi yanzun, *Nurul Huda*, idan fa ta kasance 'yata ce? Wannan tunanin ne ya sashi jin kamar zai k'urma ihu, jin zuciyarshi na barazanar tarwatsewa yasa shi kallon Junaid yace "D'an uwa ban makullin motarka zanje nan na dawo, kafin lokacin ka ida kai ma." Junaid ne yace "Amma ai ba haka mukayi da kai ba, meyasa zaka tafi ka barni nan?" Abubuwan da yake ji a kanshi yasa yaji ba ma zai iya mishi magana ba, rufe k'ofar daya fito yayi ya zagaya b'angaren matuk'i, ganin haka ba zai gyarata ba yasa Maryama cikin shak'iyanci tace "Amma d'an uwa ko gaisawa bamuyi ba sai tafiya?" Tsayawa yayi ya kalleta, wannan idon nata har yanzu dai basu sauyawa ba cewar Jibril, kai tsaye ya mayar da kallonshi ga Huda yace "Ba damuwa ai ba jimawa zanyi ba, wani abu na tuna da shi yanzun nan." Murmushi ya ma Huda yace "Nurul Huda ko? Zan dawo yanzu sai muyi hira dake." Cike da gatsali Maryama tace "Huda, zanyi magana da tonton d'in ki mijin da zan aura, ki tafi tare da waccen *Abban nanki* kafin mu gama kinji ko." Huda da har cikin zuciyarta taji dad'i da yau har mahaifiyarta ta iya nuna mata wani namiji ta kuma kirashi da abbanta, da farin ciki ta zagaya kusan Jibril daya kafe yarinyar da ido, *Abbanta*, ta tabbata dai kenan? Na shiga uku ni Jibril, yanzu wannan 'yata ce? To ya zanyi da ita? Haka kawai saina nunata a gida gida a matsayin 'yar wacce nayi wa fyad'e ko me? Junaid ma mamaki Maryama a bashi sosai jin yau tana alak'anta Huda da d'an uwanshi, to me hakan ke nufi? Gamon jini ne ko me? Da k'yar Jibril yayi murmushi ya shiga motar ya zauna, zuro hannayenshi yayi ya d'auki Huda ya ajeta mazaunin mai zaman banza sannan ya rufe, suna kallonsu har sukayi nisa kafin Junaid ya kalleta yace "Abun mamaki." Kallonshi tayi da fara'a tace "Me fa?" Ba tare daya daina kallonta ba yace "Wace irin sa'a Jibril ya zo da ita haka da har kika yarje masa ya tafi da Huda haka? Wace irin sa'a ce haka ke tattare da shi da har kika iya kiranshi da Abban Huda kuma a gabanta? Maryama ko dai da wani abu ne?" Jin yana neman harbo jirginsu ita kuma ba haka take so ba yasa tace "Ba sa'ar shi bace, taka ce, domin nayi niyyar saurarenka, sannan na shirya fad'a maka abinda ke raina a game da kai, ko da baka zo ba yau ni zan neme ka, ina so ne na fad'a maka na amince zan aure ka, shiyasa ma na so sai Huda tayi nisa da ni sannan na fad'a." Tunda ta fara magana yake kallonta cike da jin dad'in abinda take fad'a, da farin ciki yace "Mari, kina nufin kin amince zaki aure ni?" Gyad'a mishi kyai tayi alamar eh, tafukan hannayenshi yasa ya rufe fuska da su, saida yayi godiya ga Allah kafin ya bud'e ya kalleta yace "Nima maganar dake tafe dani mai girma ce, domin kuwa jiya warhaka muna cikin filin gidanku tare da kakarki muna cin abinci muna hira da ita." Waro ido tayi tace "Kakata? A ina kuka ganta? Gidanmu kuma?" Murmushi ya mata kafin ya kwashe komai ya fad'a mata tun daga labarin da Iklima ta bashi har zuwansu garinsu da kuma abinda ya faru gidansu, kuka ta dinga yi tana ji a ranta lallai son ta yake sosai, sai dai kuma ita har k'asan zuciyarta babu wani son aurenshi a ranta, son da take masa ma ba wani so bane na azo a gani, yanzun haka ta amince ni zata aure shi saboda uban yarta data gani, ko ba komai zata gasa masa aya a hannu, saita rama zalincin daya mata, saita d'and'ana mishi irin *uk'ubar* daya sata ciki shima, abun mamaki saiga Junaid sunyi hira ta fahimtar juna da Maryama, kuma duk abinda yace saita amince ta nuna ta yarda, harda cewa yau zai had'ata da dreban da zai mayar dasu gida ita da Huda, gobe kuma za aje nema mishi aurenta, bata mishi musu ba sai cewa da tayi bari taje tayi sauri su had'a kayansu. Tunda Jibril ya d'auki hanya ya rasa meke masa dad'i, shi fa daya shigo motar ya so ya samu damar da zaiyi k'wararan ihu ne da zaisa yaji sakayau , amma kuma an had'a shi da Huda, tsayawa kawai yayi bakin titi yana kallonta tana ta waige waige a cikin motar da tab'a abubuwa alamar dai kamar shigarta ta farko kenan, a zuciyarshi yake ayyana data hanyar data dace aka sameki da wannan motar zata iya zama taki wacce dreba ma na musamman gareki da zai dinga tuk'a ki, ganin kallon da yake mata yasa ta zauna tsaf ta daina tab'a komai tsoro ya bayyana tare da ita, fuskarshi ba yabo ba fallasa yace "Kina karatu?" A hankali ta kalleshi tace "Eh Abba ina yi." Wani kallon ban gane *Abba* ba? Ya mata kafin yace "Maryama mamanki ce?" "Eh Abba." Ta sake fad'a d'orawa yayi da "Ina Abbanki yake? Mamanki ta tab'a nuna miki shi?" Cikin sanyi jiki Huda ta girgiza kai tace "A'a, nima ban sani ba, amma dai yaran unguwarmu suna ce min shegiya ce ni 'yar karuwa, kuma Mamana kullum sai tayi fad'a da mutanen gidanmu idan suka ce min shegiya ce ni ko ragon suna ba'a yanka min ba, kuma idan na tambayi Mamana waye Abbana saita dinga hushi tana min tsawa da fad'a tace na tashi na bata wuri." Rintse ido Jibril yayi saboda jin hawaye sun cika idonshi har suna neman zubo mishi, *ragon suna*? Shine abinda yafi tsaya mishi, 'yar dana haifa a cikina ko bata hanyar aure bane ace ba'a yanka mata rago ba, ya ilahi, shine abinda ya fad'a k'asa k'asa, d'an bud'a idonshi yayi ya juya inda Huda take, sai gani yayi tana ta goge hawaye da bayan hannayenta wasu na biyar wasu kam, gyara zamanshi yayi ya kamo hannunta ta mik'e tsaye ya d'auke ta ya zaunar da ita kan cinyoyinshi ya fara share mata hawayen yana fad'in "Yi hak'uri kinji 'yata, ba dai yana suna tsokanarki ba? To daga yau ba zasu sake ba saboda Abbanki ya dawo, kuma maganar rago ma ki fad'a min me kike so a yanka miki, kama daga rak'umi, saniya, da kuma raguna, ke da ana yanka zaki da su gwiwa ma ni zan yanka miki." Kallonshi tayi tana dariyar jin dad'i tace "Ka zama *Abbana* daga yau?" Gyad'a mata kai yayi yana murmushi, d'orawa tayi da "Kuma duk kana da kud'in siyan wannan abubuwan?" Cike da tabbatarwa yace mata "Sosai ma, kuma ko da bana da saboda kiyi farin ciki ki wuce gori a idon jama'a ai ko bashi ne zan ci dan na siya miki." Cike da yarinta tace "Abba saniya nake so babba, kuma nafi son kalar ja tafi kyau mai manyan k'aho." Cikin dariya yace "Angama gimbiyar Abbanta." Wani dad'i ne ya kashe Huda daya sata fad'awa k'irjin shi ta kwanta luf tana k'ara goge hawaye, wata ajiyar zuciya ya sauke mai k'arfi, a hankali ya lumshe idonshi ya fata shafa kanta wanda yasha sabon kitso ya fito tsaf da shi sai walk'iyar mai yake, hakan daya faru kuma saiya zama kamar antsaga zuciyarshi an dasa mishi soyayyar yarinyar, take yaji k'aunarta na gauraya da jinin jikinshi, ba tare daya bud'a ido ba ya sumbaci kanta, cikin tausashiyar murya taji yace "Huda ki yafe min, nayi gaggawa a waccen ranar, duk laifi na na komai daya faru, mahaifiyarki ba da laifi ko d'aya." Ita dai da yau take jinta a k'irjin Abbanta yana shafata bacci ne ma ke sonyi gaba da ita, hakan ne yasa bata damu da me ya fad'a ba kawai ta sake yin shiru, ci gaba yayi da shafar kanta har yaji shirunta yayi yawa, yana lek'a fuskarta yaga ashe bacci harya d'auke ta, hak'ik'a mahaifiyarta ce tayi, daga kallon fuskarta kuma abubuwa dayawa ne suka ziyarci tunaninshi, ya zakayi da *Junaid, iyayenka ma, da ita kanta Maryama, sannan iyayenta ma da suka ganka*? Amma kallon fuskar Huda da yake sai yaji ya bashi k'arfin gwiwar tunkarar kowane irin bala'i da masifa, 'yace dai gata ta zo zo duniya, tasha wahala kafin bayyanarshi ya kuma dan da ita, amma daga yanzu daya sani har zuwa lokacin da kowa zai fahimce shi ba zai bari tayi kuka ba, shafa kanta yayi ya sake sumbatarta yace "Wannan *alk'awari* na ne gareki." Ba tare daya d'auke ta daga kan cinyarshi ba ya tayar da motar a haka ya tuk'a suka isa wata alimentation, tsayawa yayi ba tare daya fito ba kawai ya sauke gilashin motar yace babbar leda yake so a had'a mishi ta kayan da suka san zasu birge yaro, saida ya siyo suka juyo dawowa inda suka bar Junaid, shi kad'ai ya samu zaune bakin dakali Maryama ta shiga dan kimtsawa, Junaid ne ya kirata a waya ta sake fitowa, fitowa Jibril yayi da Huda a hannu ya matsa daf da Maryama zai bata ita, murya k'asa k'asa tace "Baccin farin ciki ne take na ganin mahaifinta? Ko kuma baccin wahala ne?" Da sauri ya sauke idonshi cikin nata idon da alamar tambayar me take nufi? A lokacin da zata amsheta ne tace "To ai naga kai idan har aka shiga mota d'aya da kai sai kayi b'arin ingantacciyar madarar da tana shiga mahaifa dole a tashi mutum da ita." Kallon wannan wace irin magana ce haka? Ya mata kafin shima yace "Huda, 'Yata ce?" Murmushi ta masa tace " 'Yar ka ce mana, a waccen ranar aka sameta, dalilin haka kuma na shiga karuwanci." K'asa ya kalla tare da saisaita murya yace "Ya fad'a min kuna shirin tafiya, amma dan Allah kafin ku tafi ki jira naje na dawo." Cikin makirci ta amsa mishi da "Karka damu zan jiraka, domin kuwa akwai matsalolin daya kamata mu warwaresu." Gabanshi ne ya fad'i ita kuma ta kalli Junaid dake waya da wanda yake so ya had'a shi da dreba tace "Zan shiga ciki na k'arasa shiryawa." Da kai kawai ya mata alama ta wuce ciki suma suka shiga mota suka d'auki hanya, gida Jibril yace ya aje shi, yana sauke shi kam d'akin shi ya shiga ya fito ya shiga motarshi shima, bai zame ko ina ba sai *Soura* mayanka. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Yana zuwa cikin takon rashin mutumci ya shiga hotel d'in, zuwanshi yayi daidai da Hamna na sakawa wani saurayi a cikin abokan ango lambarta a wayarshi, k'are mata kallo yayi, har zuciyarshi fa shi ya zo ne da niyyar ci mata uwar raina musu hankalin da tayi a gida, amma yana ganinta cikin ankon shagalin duka yan matan riga da siket ne jikinsu na less, amma yanda suka fitowa da da Hamna komai na jikinta saida yaji zuciyarshi ta buga, abinka ga mai yar k'iba k'irjin nan an fito dashi ya tsaya tsam-tsam, ga faffad'an k'ugun nan ya fito da kyau, d'aurin d'an kwalin dake kanta iya rabin kan kawai ya tsaya, inda manyan kitsonta na gashin doki (atach) ya kwanta a bayanta har yana kusan kaiwa a k'ugun, wani tafarfasa yaji zuciyarshi nayi, gani yake kaf mazan wurin surarta kawai suke kallo suna yabawa, jinjina kai yayi irin yana nufin zaki ci ubankin nan kafin yace " Wato ni zata rainawa wayo?" Daidai Hamna ta mik'awa saurayin wayarshi cike da jan aji zai karb'a idonta ya sauka kan boss, fad'uwar da gabanta yayi da d'aukar rawar da jikinta shima yayi yasa ta mantawa harta saki wayar bada gangan ba, saida taji fad'uwar wayar kuma tayi sauri ta kalli wayar ta rufe baki da hannu, zata sunkuya ta d'auka kuma Ammar na daf da kawowa, d'an girgiza kanta tayi a ranta tace "Wallahi wannan kallon rashin mutumci ne yake min, ba zan zauna ya kunyata ni ba cikin mutane." Ai saita mik'e ta kalli saurayin tace "Kayi hak'uri dan Allah." Fittt, ta kutsa cikin taron tana neman mafaka duk da saurayin na fad'in "Ba komai." Tsaye yayi gaban saurayin daya sunkuya ya d'auki wayarshi, kasancewar sun san juna yasa ya figzi wayar ta shi, ganin lambarta rau akan écran d'in daya fara tsagewa yasa shi goge lambar ya cilla mishi wayar, rashin sanin zai cillo mishi yasa bai rik'e ba wayar ta sake fad'uwa k'asa, rai b'ace saurayin yace "Ammar meye haka? Ya zaka fasa min waya?" Gwa da gwa ya kalleshi yace " Ita data saki ta fashe murmushi ka mata ka ce ba komai da yake mace ce ita, amma tunda ni gardi ne shine zaka nuna min karuwanci ko, to na fasa *Abdu* ci min uwa." D'aga hannu Abdu yayi yace "Allah ya baka hak'uri, wuce." Ya fad'a dan yasan shi fa k'aramin aikin shine a wurin su zubar da kwadon rashin kirki, gashi dai mutum mai ilimi da aji amma wani lokaci kamar jahili. Wucewar ko yayi ya ratsa mutanen suma, duk k'ok'arion shi na son ganota ya gagara, dan haka ya dafe k'ugu yana tunanin abinyi, duk da akwai maza wurin amma mata da iyaye sunfi yawa sai tarin yara, murmushi yayi ya nufi wajen mc dake sako baitoci, yana zuwa ya d'an mishi magana a kunne kamar abun arzik'i, hakan yasa mc d'in mik'a mishi amsakuwar (micro) d'in hannunshi ya tsayar da wak'ar dake tashi a wurin, Ammar kuma wayarshi ya ciro ya d'anyi danne danne kafin ya saita wajen sautin wayar ya jona a micro d'in, yana danna play sai ji kake *Tatatatatatatatatatatata!!!* 😂😂😂k'arar bindiga, ba mata ba da suka fashe da k'ara da ihu har maza wanda ke tsaye zaune yayi, wanda ke zaune kuma ya fad'o daga kan kujerar, yara ma ihu suka saka inda wasu kuma yaran ke ganin kawai nishad'i ne sai kuwa suke da tafi, lokacin da wasu suka rage tsayi ta hanyar durk'ushewa da yin kwance lokacin ne ya hango kankana da ita kuma tsoronta na ganinta da boss zaiyi, kallon mc yayi ya mik'a mishi micro ya kashe satin wayar tashi ya wuce wajenta, ta juya dan son ganin ina yake sai kuwa sukayi tozali. Tsoron daya gani a idonta a lokacin ya sani da zai auna jininta zaiga ya hau, matsawa yayi daga gabanta fuska ba annuri yace "Wuce muje gida." Ita kam da a gida ne tasan zata samu masu ceto, amma anan? Kuma yace su tafi gida? Tab'idjam! Hayaniya ce ta kaure a wurin na son sanin abinda ya faru, ganin babu mai kulasu hakan ne ya bata damar saka kuka tace "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri ka bari har muje gida, a kan motona na zo fa." Wani murmushin mugunta ya sakar mata tare da jerawa kusa da ita ya kama hannunta, a tare suka ji wani shocking ya baibaiye su, sororo take kallonshi tana zubo da hawaye tana ci gaba da bashi hak'uri, hankalin mutane ma baya kansu Hamna kuma har juyowa take taga ko da wanda zai iya rabata dashi, amma wak'ar da aka saka yasa hankalin kowa ya koma kan yaran dake rawar, suna fitowa ta kan matantakalar dake k'ofar shiga da ba tafi uku zuwa hud'u ba, yana saukowa daga na d'aya dana biyu ita kuma ta cije ta k'i gusawa, juyawa yayi ya kalleta, haushi ne ya sake kama shi wai akan me zata dinga fita haka tana tallar kanta a waje, k'wafa yayi tare da zagaya hannunshi ta bayanta kan cinyoyinta, d'aya hannunshi kuma ya kamo nata hannun ya wurgashi kan wuyanshi, cak ya d'auke ta ya d'ora kan wuyanshi ya nufi mota da ita, ihu take tana wutsil wutsil da k'afafu tana so ya sauke ta, boot taga ya bud'e ya nufi nan da ita, ai kuwa yana zuwa ciki ya watsata kamar buhun shinkafa, k'ara ta saki tare zunbura ta taso zaune zata mishi magana d'if ya rufe ta ya koma mazauninshi ya tayar, bubbuga k'ofar ta fara yi tana k'walla kiran yayi hak'uri dan Allah amma ina, dan ita tunaninta wani wurin zai kaita, shi kuma takaicin yanda ya sameta a wurin har tana bawa wani lambarta ne yake k'ara tunzura shi. Bai kula da tsiyarta ba har suka iso gida ya paka motar, fitowa yayi ya bud'e mata yana hararanta, tayi sharkaf da zufa ga hawaye ga majina, da k'yar ta durko ta fito takalmi d'aya a hannu da wayarta dan ky d'in moto dama yana hannun Nafi, rufe boot d'in yayi yana kallonta sai wani tank'warewa take kamar tsohuwar data gaji da duniya yace "Maza yarinya tattare min wannan shegen siket d'in zakiyi ki min tsallon kwad'i a wurin nan." Zaro ido tayi tace "Kwa me?" Dak'uwa ya mata yace "Kwad'i." Belt d'in shi ya k'ok'arin zarewa yana fad'in "Ko ba zakiyi ba?" Da sauri tace "A'a ni na isa? Zanyi wallahi." Cire takalmanta tayi d'aya ta aje gefe ta fara tattare siket d'in da k'yar saboda ya kamata, cikin jin haushi yace "Yanzu wannan da zaki saka shi uban wa ya kama miki? Duk kibi ki d'aure jikinki haka ki hana komai numfasawa, mtsssss." Ita dai ta gefen ido take kallonshi harta tattare, d'an matsawa tayi daga kusanshi ta duk'a kamar gaske zata fara, tana d'aukar takalminta sai kuwa tayi wuf da iya gudunta, kallonta yake yanda take gudun abisa gaskiyarta mazaunanta su ma na neman tsira, abun mamaki wanda ni kaina banyi zatonshi ba shine dariyar da Ammar yayi, domin kuwa duk dariya ko murmushi da yake na iya shege da da iskanci, amma wannan dariyar ta abune ya baka dariya ainin, gyara belt d'in shi kawai yayi ya sake shiga mota ya bar gidan. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ An idar da sallahr isha'i kenan Alhaji ya fito daga d'akin shi zuwa falon cikin wata dakakkiyar farar shadda da taji kud'i, hula agogo da takalma duka farare ne, Hajia na zaune a kujerarta yara na ta yar hayaniyarsu amma cikin nutsuwa, inda matan kuma ke falon sama da yan mata, lieutenant ne ya shigo da alama yanzu ya dawo daga masallaci, kallonshi Alhaji yayi yace " *Babba* kaje ka shirya ka fito yanzu zamu je wani wuri." Da ladabi lieutenant ya amsa da "To." Ciki ya shiga Hajia kuma ta kalli Alhaji tace "Ina kuma zuwa da wannan shirin?" Cikin sigar zolaya yace "Neman aure zan je, ki tayani da addu'a wannan karan na samu." Wani murmushi ta saki tace "Allah na tuba ka yafe ni, macen da zata iya zama da kai a hakan nan ai sai ni." Juyawa yayi dan bar mata falon yana fad'in "Dama kuma ke kika mayar da ni hakan." Had'e fuska tayi a ranta tana fad'in "Wallahi duk da mun tsufa ko yanzu ka ce zakayi aure saina maka tijara, dan kuwa ina k'aunar ka kuma dan ni kad'ai aka halliceka." Bai jima sosai ba ya fito cikin shirin dogayen kaya shadda kalar maroon da hula da takalmi, k'aninsu Ammar mai shekara sha hud'u wato *Kamal* lieutenant ya kalla yace "Ka fad'awa Ummynku na fita tare da Alhaji." Shi fa yayi hakane tunda sun rabu da cewa zai tafi masallaci, tunda baisan ina zasu je ba da tsawon lokacin da zai d'auke su shiyasa yace a fad'a mata, amma Hajajju sai tayi mamakin abun da ganin kamar Sa'ada na son shiga hancinta da duk'unk'une ne, da kallo ta bishi har yace mata sun fita amma ko tanke, yana zuwa ya samu Alhaji na jiranshi jikin mota, shiga sukayi suka fita daga gidan sannan Alhaji yace "Gidansu yarinyar nan Zeituna zaka kaini." Da mamaki ya kalleshi dan shi dai bai ma san gidan ba, Alhaji ne yace "Muje zan nuna maka, na tambayi Iya ta kwatanta min." Ba tare daya daina mamaki ba yace "Alhaji me zamu je yi a gidansu? Wani abu ya faru ne?" Murmushi ya masa yace "Alkairi ne zai kaimu, kuma ina fatan ba zaka watsa min k'asa a ido ba." D'aurewar da kanshi yayi yasa bai iya cewa komai ba sai kwatancen da Alhaji ke mishi yake bi kawai, da haka suka iso dama kuma ba nesa bane da su, sunyi sa'ar samun kawu Mamu a k'ofar gidan zaune ya gama cin abinci, shi ya d'auka ma Jano ne ya dawo har ya mik'e dan gaishe shi cikin girmamawa, amma duk da haka ganin manyan mutane ne saida ya gaisa dasu cikin mutumci da basu girmansu, har zai shiga dan d'auko musu kujeru suka ce ya isa nan ma, zaune sukayi suka sake gaisawa kafin Alhaji yace "... 👏👏👏 16/06/2020 à 13:21 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _10_ A cikin kwana biyu su Raihan sun gama shirye shiryen tafiyarsu tare da su Ma'awa, Abbas da kanshi ya kaisu airport saida ya ga tashinsu kad'ai ya juyo ya dawo, a kwana biyun nan kuma Ma'arufa na nan ta rasa yanda zatayi hak'arta ta cimma ruwa, bata samun wata dama ta keb'ewa dashi, da safe ma sai dai su had'u a kan dinning da dare ma haka, kuma tun anan suke saida safe sannan kowa yaje ya kwanta, hakan yasa take jin haushin Sameera sosai saboda a kwana biyun nan kuma wata irin soyayya da kulawa suke kulawa junansu, wanda hakan ya samo asali ne saboda Abbas na cewa Meerah yi kaza za tace to, a wajen Harira ma hakane sam babu fuska daga gurinshi amma duk da haka bata karaya ba kwalliyarta take cab'awa, haka kuma ya karb'o sakamakon gwajin da akawa Abdul wanda ya nuna baya d'auke da wata cutar. Yau dai Ma'arufa tayi waya da Salma kuma ta fad'a mata abinda zatayi, dan haka yau a shirye take kuma ta saka ido sosai, amma sai sauk'i ya samu saboda yamma lik'is Sameera ta fita zuwa compagninta yin wani business, kafin ta fita kuma saida ta tura yaran wajen Bilkisu dan karsu damu Ammie kafin ta fita, sam babu wanda ya tsammaci dawowarshi wannan lokacin, daga yanda yake sauri zaka san abu na gaggawa ne ya dawo dashi gidan, tunda Ma'arufa taga shigowarshi ta tafi d'akin ta da sauri dan gani tayi ba ma zata bari daren yayi ba kamar yanda Salma tace mata, tana shiga kayanta ta cire ta d'aura towel ta shafa turare sosai, wayar da suka killace domin aikin nan ta fito da ita, k'arama ce sai dai akwai d'aukar hoto rad'am ya fito ko da daga nesa ne, saisaita mata zama tayi ta yanda zata iya d'aukar komai dake kan gadon kafin ta fara sakin k'ara. Harira ma na ganin shigarshi part d'in Sameera ta bi bayanshi da niyyar tambayrshi da wani abinda yake so saboda ya ga kayan jikkinta, yana cikin bud'e d'akin Sameera dan d'aukar takardun da suka dawo dashi kawai yaji ihun Ma'arufa daga cikin d'akin ta, da sauri ya juya ya kalli d'akin da tunanin lafiya? Jin wata sabuwar k'arar yasa shi sakin makullin a jikin k'ofar ya tunkari d'akin, da zuwanshi ya bubbuga amma shiru sai ihun dake sake tashi, Harira ma dake bayanshi ta iso da sauri ta tako dan ta tambayi lafiya? Amma tana ganin ya zunduma kai cikin d'akin saita tsaya, tab'e baki tayi kafin ta fara takowa cikin sanyin jiki da niyyar shiga taga ko meye. Yana shiga ya ganta can gaban gado zaune rik'e da k'afa, k'arasawa yayi yana fad'in "Lafiya? Meya same ki ne haka?" Saboda tana so ya matso yasa ta sake fashewa da wani kukan tana fad'in "K'afa ta ce, gurd'ewa nayi zan shiga bayi." Yana zuwa gabanta yaga daga ita sai towel, kawar da kanshi yayi ya d'an kalli gadon, bai ga alamun hijabi ba dan haka ya d'auki rigar data cire yanzun ya jefa mata a jiki yace "Ki saka wannan saiki fito muje asibiti a duba k'afar nan." Wata yar banzar shagwab'a ta saki wacce ta sa shi juyowa kallonta saboda mamakin ta lokacin da take fad'in "Please Abban Khalifa ka taimaka min to na mik'e, ba zan iya da kaina ba ni kad'ai." Kallon k'ofa yayi kafin ya zuro mata hannu a ranshi babu tunanin komai sai kallonta kamar 'yar daya isa haihuwarta, tana jin ta kama hannunshi ta mik'e tsaye sai kawai ta zage towel d'in jikinta, dama kuma babu komai a jikin dan haka ta bayyana tsirara a gabanshi, shi kam yana cikin kallon k'ofa yaji alamar ta tashi, ya fara zame hannunshi daga nata yaji ta fad'o masa a jiki cikin salon k'warewa a harkar barikanci ta kai hannunta kan...Tsoro al'amarin ya bashi ta yanda ya zaburo ya kalleta, yana juyowa tayi nasarar had'a bakinta da nashi, duk da ba wani k'arfi bane ya saka mata amma yanda ya tureta yasa ta fad'a kan gadon, nunata kawai yake da hannu ya rasa me zai ce mata tsabar mamaki, da sauri ta taso ta sake kanainayeshi ta zagaya bayanshi ta zura harshenta a kunnenshi hannunta kuma cikin rigarshi, da k'arfi ya juyo gabanta ya kasheta da mari, ya nunata da yatsa yace "Ke!" Duk da marin ya shiga jikinta amma nasararta take hangowa, sake danna mishi k'irjin ta tayi ta sake sauke hannunta wannan wurin, jin harta tashe shi yasa ta kalleshi tana son had'e bakinsu tana fad'in "Karka cutar da kanka mana, kai fa ba yaro bane, kawai kaji dad'in rayuwarka." Duk tana maganar ne tana lasar fuskarshi shi kuma yana son yakicewa daga gareta cikin ruwan sanyi, dan sosai ta kama lagwonshi hakan yasa ya rasa kuzarinshi, jin ya fara mata sanyi yasa ta kamo hannayenshi ta d'ora kan mazaunanta, wai! A gaskiya duk da shi d'in ba mai sha'awar ganin mace da mazaunai bane manya amma jinsu yana shafawa yasa shi sake jin wani irin chock, tahowa ta dinga da hannayenshi sama ta sake saukewa kan boobs d'in ta, tana jin komai ya fara tafiya daidai ta zura harshenta bakinshi ta kamo na shi harshen ta fara mishi wata irin tsutsa, a d'aya b'angaren kuma kayanshi ta fara rabashi da su har ta mishi tsirara shima, Abbas dai idonshi rufe suke ruf tunaninshi ya tsaya, wacece wannan? Me nake shirin aikatawa? Matata fa? Zina ce fa? Meyasa? Bakayi haka ba ko lokacin k'uruciya, meyasa sai yanzu? Kana da 'ya'ya mata fa? Abbas farka mana. Zunbur ya zabura ya tureta daga jikinshi ya bud'e idonshi, amma dake Ma'arufa tayi niyya sai tayi saurin zubewa ta durk'ushe tayi wuf da k'asan shi sai cikin bakinta, rintse ido yayi yar labb'anshi na kakkarwa tsabar jarabar data taso mishi da ita, dafa kanta yayi da niyyar fizgota amma ina, wata irin tsotsa data masa tare da kamo waccen biyun baisan lokacin daya sake danna kanta ba, a hankali saiga Ma'arufa ta kwantar da shi kan gadon tana sarrafa shi inda shi kuma ya manta da komai ya dinga biye mata, sun jima haka jin ya kasa samun nutsuwa sai kawai ya birkitota da k'arfin shi ya mata rumfa, sabo da kuma rashin sanin takamaimai inda zai shiga yasa shi karanta addua'r saduwa da iyali, k'arfin daya zo mishi yasa mata gaba d'aya ya shiga, duk da tana yar duniya saida tasan ya ratsata, dan haka ma ta gama yarda Abbas namiji har yanzu da k'arfin shi... *Allah ka kare mana mazajenmu daga fad'awa tarkon kowace kucaka.*👏 Duk bura-ubar nan da ake Harira na tsaye har da kuka take wanda ta ma rasa dalilinsa, ita dai kawai taji hawaye na zubo mata kuma tana jin haushin abinda suke aikatawa, bata bar k'ofar ba saida taga aikin gama ya gama sannan ta bar k'ofar tana tunanin ko ta kira Sameera, wata zuciyar ta haneta da yin haka dan kuwa yau saidai su kwana a bola, dan babu abinda zai hana Sameera k'ona gidan nan sannan tayi ajalin yarinyar can wacce ita kanta take mata kallon kama da wata data sani. Kiran sallah magrib da akayi ne ya dawo dashi tunaninshi, wata firgita yayi ya sauka daga kanta ya zauna bakin gadon ya dafe kanshi, "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, la'ilaha illallah, muhammadur-rasulullahi sallalahu alaihi wasallam, hasbunallahu wa ni'imalwakil, Allahumma ajirni fi musibati, waklufli khairan minha." Addu'o'in da yake maimaitawa kenan, meya aikata? *Zina*? Meya jani haka? Bai gama tunanin da yake ba yaji Ma'arufa ta kwantar da kanta kan bayanshi tana shafa shi, da k'arfi ya tashi tare da juyowa ya kasheta da wani sabon marin daya d'auke jinta da ganinta, kasa fad'ar komai yayi sai saka kayanshi da yayi ya bar d'akin a wani mummunan yanayin da shi kanshi ba zai iya misaltashi ba, kai tsaye d'akin shi ya shiga ya wuce bed d'in shi ya cire kayanshi, toilet ya fad'a ya sakarwa kansa ruwa wanda yake jinsu kamar tafasashin ruwa. Yafi minti talatin a ciki yana kuka da dana sanin haihuwarshi da akayi a wannan rana, ya k'yamaci kanshi da tir da halinshi da bai zama namijin da zai iya kare kanshi daga aikata babban zunubi ba, kunyar iyayenshi data 'ya'yanshi ba zata bari ya sake had'a ido da su ba, bare kuma *Sameera*, wacce ba kunyarta kad'ai ba har tijararta da bala'in ta ba zai yarda tasan meya aikata ba, da wannan yanayin ne har zazzab'i ya sauko masa mai k'arfin gaske tare da ciwon kai, yana fitowa da k'yar ya iya saka dogon wando da doguwar riga fara ya kwanta ko sallah baiyi ba. A wajen Ma'arufa yana fita ta d'auke hannunta daga kuncinta ta sauko daga kan gadon ta d'auko wayar data aje tana d'auka, zaune tayi ta dubawa taga komai yayi rigimarsu ta farko ce kawai wayar bata d'auka ba kuma taji dad'in haka, save d'in shi tayi ta aje wayar ta shiga wanka zuciyarta fari tas, tana fitowa ta kira Ma'aruf tace ya zo ya d'auketa ta gama abinda zatayi, tana gama shiryawa ta had'a kayanta ta fito, a lokacin kam babu kowa data had'u da shi a falon harta fita babu wanda ya sani, tana fita k'ofar gidan kuma taga motar Sameera ta danno kai zata shiga, da sauri ta b'uya bayan gate d'in gidan, tana shiga ta fito ta nufi inda sukayi da Ma'aruf zai d'auke ta, ko da taje bata wani jira shi ba sai gashi ya zo, shiga tayi yana tambayarta ta gama komai, wayar ta bashi ya kunna ya fara kallon abinda ta d'auka, dariya yayi ya kalleta yace "Komai yayi daidai, zuwa gobe kuma wannan vidéo recoding d'in zai zama silar arzik'inmu a doron duniyar nan." Ma'arufa kuma shiru tayi dan tunanin halin da mutumin kirkin zai shiga ya d'an fara damunta, gashi basuyi anfani da kororon robar da take anfani dashi ba idan za'a kusanceta, duk yanayin saiya mata babu dad'i da haka suka isa masaukinsu. Har Sameera tayi sallah amma ba taji motsinshi ba, dan haka ta fito cikin rantsatsen less d'inta ta shiga d'akinshi, tana ganinshi kwance ruf da ciki dafe da bayan kanshi ta k'arasa da sauri ta zaune kan gadon ta tallabo shi cike da damuwa tana fad'in "Subhanallah, Abban Ameer lafiya? Meya sameka? Zazzab'i ne ma jikinka." Abbas da tunda ta shigo yaji tahowarta tana haurawa kan gadon ya ji wata tsanarshi ta k'ara zuwa mishi, k'in yarda su had'a ido yayi bai kuma bata amsa ba, shafa fuskarshi take cike da tausayi tana fad'in " *Rabin raina* dan Allah ka min magana, meya sameka haka? Mun rabu da kai lafiya fa." Tureta yayi daga jikinshi ya sake mayar da kanshi kan pillow, ba tare da damuwa ba ta sake d'auko kanshi ta rumgume tsakanin k'irjin ta tana fad'in "Na kira maka dr Kabir ne ya duba ka?" D'an k'aramin tsaki yayi ya sake d'auke kanshi yana fad'in "Mtsss, leave me alone." Gyara mishi kwanciya tayi tace "Ina zuwa, bara na d'auko wayata saina kira shi." Ta juya kenan taji muryarshi yace "Bana so, karki kira min kowa, kema dan Allah ki barni ni kad'ai, please and please." Mamaki ne ya sakata dawowa kan gadon ta juyo dashi tace "Abban Ameer, lafiya? What it's problèm?" Ba tare daya bud'a idonshi ba cikin wata irin muryar data kasa fahimta yace "Na ce ki fita kema, bana so kowa ya dame ni dan Allah." Cikin d'an daga murya tace "Ban gane baka san kowa ya dameka ba? Meya faru ne? Me akayi maka a gidan ko a waje? Matsalarka har ta kai k'adamin da ba zaka iya fad'a min ba? Ni fa mata...." A hassale ya mik'e ya sauka daga kan gadon ya fizgi hannunta yayin da hawaye ke zubo mishi a idonshi na k'una zuci ya nufi k'ofa da ita, kallon fuskarshi take da mamaki tana ganin hawayen dake zuba, tabbas tasan yana kuka kuma yana son zama shi kad'ai idan ya tuna da yanda mahaifinshi ya rasu, amma ganin wannan zunzurutun damuwar kam ita dai bata tab'a gani ba, yana shirin fitar da ita daga d'akin ta cije ta fincike hannunta tace "Wai meye matsalar, dan Allah Abban Ameer ka fad'a min, kasan hankalina ba zai kwanta ba idan har baka fad'a min ba? Ni dai a sani na ban aikata maka wani laifin ba, amma..." Zafin zuciya da halin da yake ciki na tashin hankali da jin zai iya dukan koma waye ya d'auke ta da mari, bai bari ta gama fahimtar meya faru ba ya jata zuwa waje yana fad'in "Ke har abada ba kya fahimar halin da mutum ke ciki." Yana jefata waje ya mayar da k'ofar ya rufe da makulli, Sameera dake dafe da kunci tsananin mamaki take, toh! Me yayi zafi haka? Laifin waye ya shafeta da har Abbas zai iya marinta? Meye damuwarshi? Rashin sanin wannan amsoshin yasa taja k'afa jiki a sanyaye ta bar wurin ta koma d'akin ta, ita ma bata sake fitowa ba saboda tunanin damuwar dake damun mijinta, Ammie ma da taga shiru ta d'an damu, kuma ga duka motocin gidan bare ta d'auka sun fita, amma haka ta daure saboda tunanin kusanci na mata da miji. *A kwana biyun nan* sosai Fadila ke sakewa suna hira ta waya da Saleem, inda yake rubtata ita kuma tana fad'a mishi komai daya shafesu, a haka ya zurmata har ya fahimci tana kishi da Raihan wacce ita bata ma damu da abinda ita Fadilar ta damu da shi ba, nan fa ya nuna mata zai mata maganin matsalarta ta yanda shi zai samu Raihan, dan shi yana nuna mata yana son Raihan ne har zuciyarshi, ita kuma zata samu Abdul ita kad'ai, abinda yace tayi ne ya d'an sata jin wani iri haka, amma daya k'arfafa mata gwiwa ya nuna mata ta haka kawai zata samu soyayyar Abdul, sai kawai tace zata k'ok'arta ta gani, amma fa dan Allah karya cutar da Raihan d'in, murmushin jin dad'in samun nasara yayi yace karta damu, shi fa sonta yake kuma zai iya komai danya sameta. To fa a hakane yanzu Fadila take sakawa Raihan d'in ido duk wani motsinta, yau ma dawowarsu kenan tare da amarya daga wurin gyaren jiki, d'akin uwar amarya *Kubra* suka shiga kowace ta fara k'ok'arin wanka, dayake babban gida ne kuma da ban d'aki dayawa sai kowa bai tsaya jiran d'an uwansa saiya fito ba, Raihan ce tayi nasarar shiga toilet d'in aunty Kubra, babu kowa a d'akin dan haka tana shiga Fadila ta dawo d'akin, tana ganin ta shiga tayi sauri ta fita ta zagaya bayan d'akin, doguwar kujera ta samu ta taka ta lek'a ta window, ai kuwa saiga Raihan ta bayyana tana cire kayanta, sabuwar wayarsu ta d'auka ta danna camera ta fara d'aukar ta hoto, Raihan dake wanka tana jin dad'in saukar ruwan daga sama idonta rufe, saida ta d'auki tsiraicinta kad'ai ta sauko ta dawo d'akin ta aje wayar ta shiga wanka ita ma. Saida suka ci abinci suna zaune ta shiga WhatsApp ta tura ma Saleem wannan hotunan, yana ganin hotunan saida yaji wata sha'awar yarinyar, amma haka ya daure yana ta kallo har saida ya samu nutsuwa. *Washe gari* abun alajabi suka tashi da shi, bak'uwar gidansu babu ita babu labarinta, kuma babu wani abu data bari da zai nuna taji dad'in zaman gidan ko tayi godiya kan abubuwan da aka mata, haka Ammie ta dinga mita akan tafiyar ta ta tunda babu kayanta, da safe ma haka Abbas ya tashi babu k'warin jiki, wanka yayi ya shirya cikin manyan kaya, maimakon ya fita saiya koma ya zauna yana jin kunyar fita, Sameera ma data ga har yara sun tafi makaranta amma bai fito ya karya ba yasa ta d'auki abun karin na shi ta shida part d'in shi, a falo ta ajiye a k'aramin center table ta nufi bed d'in shi, a hankali ta bubbuga amma shiru, sake bubbugawa tayi daga ciki yace "Please Sam ki barni dan Allah, na fad'a miki bana son takura." Cikin muryar rarrashi tace "Dan Allah Abban Ameer ka bud'e min k'ofar nan, ka sani fa baka da wanda zaka fad'awa damuwarka sama dani, idan kuma ba zaka iya fad'a min ba to ka fad'awa Abba ko Ammie mana, amma kana gani gaba d'aya ka saka kowa damuwa, yara sun tafi islamiyya babu farin ciki saboda basu ga Dadynsu ba, Ammie tana tambaya ta lafiyarka k'alau? Bansan me zan ce musu ba." Daga ciki ya amsa da "Ki fad'a musu bana jin dad'i ne kawai." Sanin ba zai bud'e ba yasa tace "Shikenan, zanje na fad'awa Ammie komai ita idan ta zo nasan zaka bud'e, ba zan fad'awa Abba bane dan nasan idan ya zo zai karya k'ofar ne." Da sauri ya taso yana fad'in "No Sam, please." Jin yana bud'ewa yasa ta tsaya tana kallon k'ofar, yana bud'ewa sukayi ido hud'u da shi, damuwa ce karara kan fuskarshi, saidai ya k'i kallon fuskarta har yanzu, ajiyar zuciya ta sauke tace " Muje ka ci abinci gaya nan falo." Juyawa yayi ya d'auko wayarshi da makullin mota sannan ya dawo, wucewa yayi kamar wani gunki harya zauna kan kujera, durk'usawa tayi gabanshi ta fara zuba mishi abincin, harta gama bai kalleta ba saida ta ajiye mishi gabanshi, cokalin ya d'auka zai fara ci amma sam baya da appétit, da k'yar ya daure ya rufe ido zai kai loma bakinshi wayarshi tayi k'ara, cike da rashin kuzari ya d'auki wayar ya duba, bak'uwar lamba ce dan haka ya k'i d'auka saida aka sake kira na biyu shi ma bai d'auka ba, amma dake Salma ta fad'awa Ma'arufa komai game da shi saita turo mishi text kamar haka _"Ka d'auki waya zamuyi magana ne, very importante."_ Bai wani damu ba dan in bai d'auki wayar ba dama text ake turo mishi, ana sake kira ya d'auka ya kara a kunne, muryar Ma'arufa ce a kunnenshi tana fad'in "... *More comment plsss* 16/06/2020 à 13:22 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _16_ "Iya wani zunubi zuciyata ta aikata wanda ko a mafarki bai dace ace nayi ba bare kuma a zahiri." Dafe k'irji Iya tayi tace "Ke 'yar nan! Me kika aikata haka? Allah yasa dai ba wani mummunan bai abu kikayi ba." Alhaji da farko juyawa yayi tunda yaji tace sirri ne kuma bai kamata ace yaji ba, amma jin tace zunubi kuma saiya dakatar da shi, *zuciya* kuma *zunubi* murmushi yayi ya tsaya dan yasan duk inda zancen zaije ba zai wuce maganar soyayya ba, sai dai yana so yaji meyasa matashiyar ke tunanin zunubi zuciyarta ta aikata? Ko dai irin *wahalalliyar soyayyar* take? Soyayyar da babu sakamako mai kyau a cikinta saina wahala da dakon abinda baya anfanar da gangar jiki bare ita kanta zuciyar, dan haka ya tsaya dan jin matsalarta. Kallonta tayi a marairaice tace "Iya mummunan abu ne kam, dan idan akaji zata min alawadai, wasu kuma zasu min dariya saboda ganin matsayina bai kai can ba, kuma nima nasan da haka Iya, jarabawa ce kawai wacce take neman tafi k'arfi na." Cike da tsoro Iya ta dafata tace "Zeituna, a sanin dana miki ba kya da wasu miyagun halaye, amma maganganunki sun d'ugunzuma tunani na zuwa kwokwonto da son jin zunubin da kika aikata, fad'a min wane irin zunubi ne wannan." Cikin zubo da hawaye tace "Iya na kamu da so, son wanda bai kamata ace na kamu da son shi ba, son mutumin da ba zai tab'a kallon ko da fuskata ba bare ya ji wani abu mai kama da so a zuciyarsa a game da ni, son mutumin da ko da ace 'ya ce ni mai gata yafi k'arfi na saboda wasu dalilai, Iya bansan ya zanyi ba dan Allah ki bani shawara?" Cike da kulawa ta kalleta tace "Zeituna har yanzu a duhu kike saka ni, ki fito ki fad'a min matsalarki, kin manta na fad'a miki ke kamar 'ya ce a gurina?" Gyad'a kai tayi alamar eh kafin Iya tace "Dan haka Zeituna karki sare, ke fa 'ya mace ce, kina da damar da zaki so kowa kuma kowa ma ya so ki, karki k'ask'antar da kanki har ki dinga ganin baki dace da samun soyayyar wani d'a namiji ba, ke nifa na yarda da yata wallahi, tsaye da kyau haka zaune da kyau, har waye zai ce ma baya sonki? Ai ki k'addara koma waye to shi yayi babban dace da har samu nasarar samun soyayyar ki, dan haka fad'a min naji waye shi?" Cikin murmushin jin dad'i na yabon da Iya tayi mata ta kalleta sororo tace "Iya Abban Ammar ne, mijin aunty Sa'ada, lieutenant Hassan Gaga." Har gaban Iya saida ya fad'i a wurin, zaro ido tayi lokaci d'aya kuma dan karta sanyaya mata gwiwa taji ba dad'i sai kuma ta wayance tace "Haba dai? Dama ai na fad'a miki koma wanene shi yayi dace ba ke ba, ke baki ga banbancin dake tsakaninku da shi bane?" Da mamaki Zeituna ta kalleta tace "Wane irin banbanci Iya? Lieutenant fa nace miki na gidan nan, mahaifinsu Ammar." Da yar harara ta bita irin ta yo shi d'in fa kafin tace "To sai me? Tabbas yana da kud'i da kuma ilimi, amma duk da haka akwai abinda ke ma kika fishi." "Me kenan Iya? Cewar Zeituna da har yanzu take mamaki. Murmushi Iya tayi tace "Kin fishi k'urucuya, Zeituna ke yarinya ce shi kuma tsoho, hakan zaisa ba zai iya juyawa soyayyarki baya ba." Rufe ido Zeituna tayi irin wai kunyar nan tana fad'in "Kai Iya, Allah ba tsoho bane." Waro ido Iya tayi tace "Iyeeh! Kaji min yarinyar zamani ko, to zan gani idan ba tsohon bane." Had'e murmushin kan fuskarta tayi tace "Iya zan bar garin nan." "Me? Barin gari? Meyayi zafi? Ke duk zafin soyayyar ne? Zeituna karki halaka kanki mana, ki bi komai a sannu kina kai kukanki wajen ubangiji, nima zan tayaki da addu'a." Duk iya tayi maganar ne tana kallonta. Girgiza kai tayi tace "Iya ba wannan bane matsalar, matsalar kawu Mamu ce." Nan ta kwashe komai ta fad'awa Iya wanda taji suna tattaunawa, kuka take sosai Iya na rarrashinta da cewa tayi hak'uri kar tayi saurin barin gari tunda babu inda zata je, sun jima nan zaune suna tattaunawa har Alhaji ya bar wurin cikin matuk'ar sanyin jiki, d'akin baccinshi ya shiga ya zauna kan kujerar da bata da maraba da gado yana tunani, hak'ik'a *so* wani abu da babu wanda ya bari, babu ruwanshi saiya shiga zuciyar babba komai girmansa ya kuma gaura shi a k'asa, haka kuma ya shiga zuciyar matashi komai k'uruciyarshi yayi maganin wautarshi da rashin hankalinshi, tunanin Zeituna da halin da take ciki ne ya tsaya masa a rai, kawun ta? Amma baya tsoron mahallicinsa? 'Yar d'an uwanka zaka nemi ka jefa rayuwata a harkar karuwanci? Da wannan tunanin Alhaji ya jima zaune ya kasa yin komai har saida ya samu tsayayya kuma gamsashiyar shawara sannan ya mik'e ya shiga wasu harkokin. Da safe bayan sun karya Hajia tace lieutenant ya kira colonel ya sanar da shi gobe zasu je Goure neman auren Maryama, haka kuma ya kira gwamna ya sanar dashi an tsayar da auren 'yarsa Amna, yanda tace haka yayi hakan yasa colonel daya samu sararin aikin kiran da aka mishi ya d'auko mota ya kamo hanya tare da masu tsaronsa a biye da shi. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Tunda suka je asibiti ko aiki ya had'a su Ummy ta k'i yarda ko ido su had'a, ya fahimci hushi take dashi abinda ya tsana kenan a duniya, yawan sakawa Ummy na fushi dashi yasa yake k'ara jin haushin Hajia shima, har lokacin tashin shi yayi ya shirya ya fito, har zai wuce ta gaban d'akin inda ake kwantar majinyata saiya hangeta tana cirewa tsohuwar da yasa a kwantar da ita saboda tana neman agajin gaggawa, turo k'ofar yayi ya shiga babu sallama, juyowa Ummy tayi tana ganinshi ta d'auke kai, amma saboda dokar aiki da kuma ba kowa yasan d'a da uwa bane yasa cikin dakakkiyar murya a harshen fransanci tace "Docteur har ka fito? Na ga lokaci ya d'an ja kuwa." Saida ya kalli robar ruwan ya kalli tsohuwar ya zauna bakin gadon kusa da tsohuwar yana kallon fuskarta yace "Kaka ya jikin naki?" Kallonshi Ummy tayi, wato ba zai kulata ba dan ma ya samu ta mishi magana? K'wafa tayi a cikin zuciyarta ta juya da wani d'an kwano kwano kuma shi ba faranti ba a hannunta wanda ake zuba 'yan magunguna da allurai zata fita, ji tayi yace "Madame jira." Tsayawa tayi ta had'e wani abu a mak'oshinta kafin ta juyo da fara'a a fuskarta, a lokacin kuma tsohuwar ta amsa mishi da "Jiki da sauk'i likita." Fuskar dai a yabo ba fallasa yace "Ina fatan dai baki manta duk abubuwan dana fad'a miki ki kiyaye ba ko?" Cikin murmushi tace "Ban mance ba likita." Mik'ewa yayi ya dauk'i abun sauraron bugun numfashi ya dinga d'ora mata a k'irji, ajewa yayi akan farantin dake hannun Ummy ya d'auki abun awon hawan jini ya zura mata a hannu ya d'aure mata ya danna wani madanni, nan ma saida ya samu sakamakon da yake buk'ata kafin ya d'an duba idonta, katinta dake aje kusan kanta ya d'auka ya duba tare da wasu yan rubuce rubuce, takardar maganin daya bata tun farko ya sake nuna mata yace "Kaka ki tabbatar an siyo wannan magungunan fa." Gyad'a mishi kai tayi tace "Yaron nawa ma yana zuwa yanzu zan bashi ya siyo." Murmushi ya mata wanda ya ba Ummy mamaki, tana tsaye tana kallon shi ya d'an dafa kafad'ar ta yace " Da kyau kaka, Allah ya sawak'e ya kara afuwa." Kallon Ummy yayi yace "Madame idan yaron nata ya zo ku tabbatar kun bashi ya siyo maganin, idan ya kawo ku nuna mishi yanda zatayi aiki da shi babu jinkiri, daga bisani sai ku sallame ta, amma zata dawo nan da sati biyu." Ummy ita tasan kawai bura uba ce yake mata, amma haka ta daure tayi murmushi tace "Ok docteur, za ayi yanda ka ce." Wani d'aure fuska yayi yace "Haka nake so." Cikin takon k'arfi ya fita ya shiga motarshi, da kallo tsohuwar ta bishi tayi murmushi tace "Allah sarki likitan babu ruwanshi, Allah ya mishi albarka." Kallonta Ummy tayi a ranta tace "Bala'i, tsohuwa dan baki san shi bane shiyasa kika ce haka." ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Ana idar da sallah la'asar Hamna ta shirya cikin kayan makaranta da kuwa jakarta, saida ta sake jadaddawa Amna tsarinsu tunda ita ba zata tafi ba, a tsorace dai Amna tace "Dan Allah karki jima kiyi sauri ki dawo, kinsan fa in suka gane zan sha masifa a gurin Hajia." "To naji dan Allah." Ta fad'a alamar matsuwa, fitowa sukayi falon Hajia na zaune, ganin kayan makaranta a jikinta yasa Hajia ta bita da kallo kawai bata hanata fita ba, Amna dake nesa da Hajia zaune tana kallo ne ta kalla tace "Ke kuma ba zaki je makarantar ba ne kome?" Murya a tausashe tace "Hajia yau zamuyi hadda ne na alk'ur'ani, ni kuma kwana biyu kenan bana tab'a Alk'ur'ani shiyasa ba zan je ba." Shiru tayi mata Hamna kuma na jinsu amma ta fice abinta, a motonta ta tafi ba jimawa ta isa gidansu k'awarta *Nafi*, tana zuwa ta cire kayan makarantar nan ta shiga tsarawa kanta kwalliya, sun d'auki lokaci suna shiryawa kafin suka gama suka d'auki hotuna, yamma lik'is suka hau moton dan zuwa wajen kamun k'awarsu da akeyi yau wanda gobe ne d'aurin auren, a cikin *hotel jangwarzo* ne dan haka basu wani jima ba suka iso. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Sai bayan sallah azahar ya dawo gidan bayan ya ci abincinshi a waje, dan rabon da yace ya ci abincin gidan nan harya manta, yana zuwa kayan jikinshi ya cire ya watsa ruwa ya kwanta, ba jimawa kuma bacci mai dad'i ya d'auke shi, kiran sallah ne ya farkar dashi dayake akwai babban masallaci wanda ya kasance na gidan ne dake kallon juna da gidan, a kasalance ya tashi yayi alwala ya tafi masallacin ya dawo, yana zuwa ya samu kira a wayarshi rutu-rutu, baiyi tunanin mayarwa ba ya nufi ban d'aki dan yin wanka, wani kiran ne ya sake shigowa wayarshi ya dawo ya d'auka yana tsaki, daga can b'angaren aka ce "Anyi walk'iya mun ganku, yanzu Ammar mu zakawa rashin mutumci?" Saida ya zauna bakin gadon cikin muryar bacci yace "Idan kana son gani na ni ko ba ayi walk'iya ba zaka iya haskani da fitila, rashin mutumci kuma yanzu na fara darza muku shi, kafin nan fad'a min dalilin kiran nawa?" *KB* da yasan halin kayanshi ne yace "D'an iska kana nan da halinka, indai za'a fad'a to sai ka fad'a kai ma." Kamar bashi da lakka yace "Ai ni na wuce ka kirani d'an iska, sai dai d'an rai-rai (sahara), malam muryarka na damuna fad'a min meya faru." Kb ne yace "Domin Allah Ammar tun yaushe muka fad'a maka da bikin *Abdullahi* ya taso? Tun shekaran jiya aka fara k'unshi amma bamu ga k'eyar ka ba, yanzu ma muna shirin tafiya wajen kamu ne nace bara na kiraka dan naga iskancin naka ba mai k'arewa bane." Yana d'an tattausa wuyanshi ya lumshe ido yace "Ni ne zaku gayyata wani wai k'unshi? Kawai muyita yawo a rana wai zamu je d'aukar abinci kamar 'ya'yan da aka haifa lokacin hamada (yunwa), sannan yanzu kamun me zanje? Idan naje uban wa zan kama? Amaryar ko ango? Kaga malam nifa bana cikin wannan salon 'yan banzancin, ranar d'aurin aure naje na shafa fatiha dani." Tab'e baki Kb yayi yace "Shikenan, idan baka zo ba ai nasan 'yer uwarka ta zo ita, dan duka k'unshin da akayi na ganta har ma tana kirana da yayanta, na d'auka ma kai ka fad'a mata ni abokinka ne." Ba tare daya bud'e ido ba ya d'an saka hannu ya murzasu yace "Saboda ubanka ne shugaban k'asa saina zauna ina fad'awa mutane kai abokina ne? Ni na ma tab'a fad'a maka ina da yer uwa a duniyar nan?" Jin dariyar da Kb keyi yasa ya kashe wayar ya mik'e ya shiga wankan shi, amma yana shiga sai zuciyarshi tace mishi "Wacece kenan?" Tunani ya fara kan wacece a cikin yan matan, wani dogon tsaki yayi jin zuciyarshi ta mishi katsalandan da fad'in "Indai ba Hamna bace can su suka sani." Tsakin da yayi yasa yace "To ina ruwanka inma ita ce? Can ta k'arata mana, wannan dama ai kullum cikin yawon biki da gidajen k'awaye take." A haka ya fito daga wankan ya shirya cikin bleue riga da bak'in wando, yana d'aukar makulli da waa ya fito ya tunkari wurin aje motoci, amma sai ji yayi yana son yasan wacece a wurin taron, dawowa yayi ya shiga yar farfajiyar da zata sadaka da falon Hajia, tun anan ya ga Jamila tare da Zeinabu da kuma Soueiba da kaka Husseina, wucewa yayi yana fad'in "Barka." Inda Jamila ta bishi da "Ina wuni yah Ammar." Kamar bai ji me tace ba haka yasa kai falon, yana shiga kuma yayi daidai da fitowar Umaima da alama bata jima da dawowa daga aikin ba wanka ne tayi, ita ma bai sake bi ta kanta ba duk da tana fad'in "Ina wuni yah Ammar." Saida ya wuce ta murgud'a baki tace "Surukantaka da irinka ai asara ce wallahi." Hajia na zaune kan kujerar da kullum anan kake ganinta tana kallo da remote a hannunta tana canza tasha, kallon tvn yayi ya ga film ne na turanci tsagwaronsa amma ko ta kafe tvn da ido, murmushin jin haushi yayi ya wuce yana fad'in "Ki ba kanki lafiya, ke ba ji kike ba kuma ki tsura musu ido kamar mai ganewa." Da kallon banda lokacin ka ta bishi tace "Uwarka nake jira ta zo ta fassara min." Wayarshi dake hannunshi ya nuna mata yace "Na kira miki ita ne tayi sauri ta k'araso?" K'wafa tayi dan tasan yanzun sai ranta ya b'ace a banza a wofi, ganin ya tunkari sama inda d'akin su Amna yake yasa ta d'aga murya tace "Kai me zaka je yi musu a d'aki? Jarabarce ta motsa ko? To fito daga nan kaji na fad'a maka, duk gaggawar ungozuma ai ta bari a haihu." Wani murmushin shak'iyanci ya sake mata yace " To Hajajju mutan makka banda abinki jaraba ta motsa ai dole na samu inda zan d'ura ta, addu'arki kawai nake buk'ata ina zurawa na zura kan daidai ta yanda ba zan fito daga d'akin nan ba saina samo miki sabon shalele, ko ba komai kinga kya rabu da waccen gardin da kike kira shalele." Hajia rasa amsar da zata bashi tayi sai kawai tace "Zan iya d'aga maka k'afa kan duk iskancin da zakayi a gidan nan, amma wallahi karka kuskura kayi gigin kawo min d'an gaba da fatiha, ba zan lamunci haka ba, kuma dama na jima da sanin cewa kana hassadar soyayyar da nakewa shalele, ka ka ci kanka wallahi." K'ala baice mata ba ya k'arasa ya bud'a k'ofar d'akin kawai ya shiga ba tare da neman izini ba, Amna da fitowarta daga wanka kenan tana zaune bakin gado zata shafa mai, duk da towel d'in jikinta kakkaura ne kuma ya sauko har kan gwiwarta, amma tsananin tsoratar da tayi ba kad'an bace, yanda ya shigo d'akin take mamaki, a saninta dai anyiwa samarin gidan kashedi (interdit) da shiga d'akin yan matan haka kawai, suma kuma yan matan basa zuwa b'angaren su saida dalili, shi kanshi saida ya shigo d'in yaji yayi nadamar shigowa, dan kuwa mutanen k'asan nan da Hamna ta so tayarwa tunda safe sune yanzu Amna ta tayar daga kwanciyarsu, amma dayake masifa ce ta kawo shi sai yayi kamar bai wani damu ba ko yasa abun a kai, k'arasowa yayi ya rufe k'ofar ya tsaya gabanta, Amna data kasa tashi sunkuyar da kai tayi gabanta na bala'in bugawa da k'arfi, wata irin tsayuwar rashin d'a'a ce ya mata ta yanda da zai sunkuyo to fa kansu na iya had'uwa, tun daga nan ya tabbatarwa kanshi da Hamna ce dan wani lokacin baka iya tantance su duk da akwai d'an banbanci amma ba mai yawa ba, amma danya kamata sai yace "Ina Kankana." Wani irin zabura da taji zuciyarta tayi yasa ta d'an dafe k'irjin ta ta rintse ido, cije hak'oranta tayi a ranta tace "Shikenan Hamna kinja min masifa ina zamana, da nasan shi zai nemeki wallahi da ban yarda da abinda kika fad'a min ba, ohh ni, *tawa ta same ni*." Wani tsinannen rank'washi (k'ozo) ne daya sakar mata a kai har saida taji jinin al'adarta ya bulbulo da k'arfi, cikin d'aga murya yace "Ba dake nake magana ba, 'yar banza kai mai zubin mage, kina ji ina magana zaki min shiru." Dafe kai tayi ta fashe da kuka bilhakk'i tana fad'in "To yah Ammar ai..." Shirun da tayi yasa yace " Ai me? Fad'i ina jinki ko na cire miki hanci yanzun nan." Cikin kukan tare da d'aga murya dan ta samu mai kawo mata agaji tace "Ni ce fa." Sunkuyawa yayi ya lek'a fuskarta hakan kuma yasa har saida numfashinsu ya gauraya, dayake ta gama wanke bakinta ne ta fito kuma ta d'auki turaren baki mai fitar da k'amshin ayaba yasa kamar ya cabki bakinta ya tsotsa, ita kuma d'an kawar da kanta tayi gefe, cikin wata irin murya yace "Ke ce kankana kike nufi?" D'aga kai tayi da sauri alamar eh, jinjina kai yayi dake nufin ok zaki sha mamaki, mik'ewa yayi daga sunkuyon yasa hannu ya fara cire d'amarar k'ugunshi (bel, ceinture), a matuk'ar firgice ta kalleshi dan ganin me yale shirin yi, yana zage shi gaba d'aya ta zabura ta mik'e zata zuba a guje, hannunta ya rik'o tare da wurgata kan gadon ta fad'a kwaram, a lokacin ne kuma idonshi suka sauka kan jinin daya d'an fara b'ata zanin gadon, dan ko audigarta bata saka ba ta tsaya shafa mana, wani tarrr yayi da idonshi ya nuna mata wurin da yatsa yace "Ita sarauniyar shan kankanar nasan dai aman ruwa take🙆‍♀️, ke kuma kenan na jini kike?" Girgiza kai tayi ba tare data daina kukan nan ba, sake dungure mata kai yayi yace "Dan ubanki ki min shiru, magana ce fa kawai muke ban kai ga dukanki ba." Tsaf ta had'iye kukan tana wik'i-wik'i da ido, d'orawa yayi da "Amna ni k'aramin yaro ne?" Kai ta girgiza mishi da haka yace "To meyasa zakiyi tunanin raina min hankali? Shin kinsan tayaya d'azu nasan cewa kina fashin sallah?" Ita dai da kai kawai take amsa mishi, ci gaba da cewa yayi "Shine har zaki nuna min kanki a matsayin kankana, kenan ni sakarai ne mahaukaci? Haka ranar ma tayi shiga irin taki taje min dan na bata wayarta, shine yanzu ma ta fita daga gidan da niyyar idan wani ya tambayeta kice ita ce anan ke kuma a can." D'aga belt d'in yayi da niyyar tsorata ta kawai, amma Amna da tsoro ya mata waya sai tayi wuf da Ammar ta rirrik'e rigarshi ta d'ora kanta a k'irjin shi tana fad'in "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri." _Ai ko malam ko uba zai dakeka kayi wuf da shi to ka gama dasu aradu, bare wani Ammar😏, nifa wannan karan bana yinka._ Sanyin da jikinshi yayi yasa shi sakin belt d'in bai shirya ba, lumshe ido yayi saboda tula tulan nonuwanta da suka zauna daram kan k'irjin shi, take yaji daga k'asa anyi wani ziiiiiii da yasa shi cewa "Ya salam." Ba tare daya bud'a ido ba cikin kasalalliyar murya yace "Amna ya kike so dani? Na mutu?" Jin wata tattausan murya da bata tab'a ji ba yasa ta d'ago kanta, da sauri ta matsa baya ta saki rigarshi a d'an tsora ce, k'asa tayi da kanta cikin muryar kukan shagwab'a tace "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri karka dake ni, wallahi ba laifi na bane, Hamna ce tace nayi inba haka ba wai saita ja min matsala wajen Hajia, kuma ni nasan zata iya saboda tana yin kamar ni wani lokacin tayi abu." D'ago kai tayi ta kalleshi, duk da wani sabon yanayi ta gani a tare dashi, ya wani saki ido dabaki yana kallonta kamar ya fizgota jikinshi amma haka ta daure ta sake marairaicewa tace "Kayi hak'uri dan Allah, ba zan sake ba." Belt d'in shi ya nuna mata da ido yace "Mik'o min." Da sauri ta d'auka amma da zata mik'a mishi saida ta ja baya, karb'a yayi tana kallo harya mayar a k'ugunshi, cikin amon muryar data kasa fahimta yace "Ai nasan inda take, zanje can na sameta na yanka mata kazar wahala sannan na d'auko ta." Juyawa yayi da sauri harya bud'e k'ofa kuma ya juyo ya kalleta yace "Wallahi na bada baya kika kuskura kika kira kankana kika fad'a mata ina zuwa, hummm." Saida ya gyara tsayuwa yace "Kinsan me zan miki?" A hankali ta girgiza kai, ba yanayin wasa a fuskarshi yace "Wallahi zaune zanyi na b'ata lokaci wajen cire miki duk sinadaran dake jikinki, kin gane?" D'aga kai tayi kawai almar eh amma ba tare data fahimci sinadaren da yake nufi ba, yana fita ta sauke ajiyar zuciya tace "Yanzu da shine ake nufin nayi rayuwar aure? Amma tayaya?" Yana fita baibi ta kan Hajia ba ya fice daga gidan ya nufi hotel d'in dan d'aukar Hamna... *Bébé Abdul latif ba lafiya, addu'arku masoya*👏 17/06/2020 à 11:45 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _18_ "Ni sunana Alhaji Suleymane Gaga, wannan kuma babban d'ana kenan mai sunan mahaifina, *Hassan*, amma ina kiranshi da babba, a gidana 'yer d'an uwanka Zeituna take aiki, kuma mun zo ne akan maganarta yanzu haka." Kallonsu yayi dukansu kafin yace "Alhaji kace manyan bak'i ne ku? Ai duk garin nan babu wanda baisan da zamanku ba, Gaga, Gaga, ai suna ne daya zaga ko ina a fad'in garin nan dama kewayenshi, sai dai kuma kun saka zuciyata cikin rud'u jin kunce kun zo akan maganar Zeituna, dan Allah idan laifi tayi ku dubi Allah ku yafe mana, karku ce zakuyi shara'a damu ko kuma ku rufe ni, ita da tayi laifin can ku hukuntata saboda yar banzar yarinya ce bata jin magana." Lieutenant da bai fahimci komai ba kallon mamaki yake wa tsohon (dan kuwa ba zaka kirashi da dattijo ba), ance yar d'an uwanka, amma ka ce ita a hukunta ta kai a rabu da ka, to wane irin rik'o kake wa yarinyar? Alhaji ne yayi murmushi wanda shi jin haka bai dame shi ba idan aka kwatanta da abinda yake shirin aikatawa, cikin lumana yace "Ko d'aya, babu laifin data aikata, mun dai zo neman aurenta ne idan har za'a bamu." Zabura yayi yana fad'in "Me? Aurenta? Zeitunar? Ku kuwa me kuka gani a jikinta da har zaku zo neman aurenta alhalin kuna manyan mutane haka kuma masu kud'i, wai ko dai ba Gagan da nake ji ana fad'a ba har a redio mai masana'antu da dama?" Wani murmushin dattako yayi yace "Ni ne da kaina, idan kuma kana son k'arin haske saina maka dalla dalla yanda zaka fahimta." Shi fa a saninshi yayanshi duk masu mulki da iko ne, ni kam ina zance ya min dalla dalla nasan ko da sojan cikinsu zai had'a ni, dan haka kawu Mamu yace "A'a Alhaji, ina dai mamaki ne, amma to wa yake son Zeituna da har ka zo neman mishi aurenta?" Jim Alhaji yayi ya d'an sauke wata sanyayyar ajiyar zuciya ya kalli lieutenant dake kallon bakin Alhaji yaji wa zai nemawa auren wannan k'azamar yarinyar, kallon kawu Mamu Alhaji yayi ya nuna lieutenant yace " *babban d'ana* Hassan." A tsorace lieutenant yace "Me? Ni kuma?" Wani kallon karka mayar da ni k'aramin mutum Alhaji ya mishi kafin ya kalli kawu Mamu dake shima yake kallon lieutenant yace "Karka damu, bai d'auka abinda zan fad'a ba kenan." Kawu Mamu kuma shi sam shekaru ko yayan mutumin ba shine a gabanshi indai har zai samu kud'i, to amma matsalar su aure ne ya kawosu bare yayi tsammanin samun kud'i dayawa daga garesu da suka zarce na Jano, dan haka kawai sai yace "A gaskiya Alhaji ba zai yiwu ba, domin kuwa Zeituna na mata miji, aure zan mata." Murmushi Alhaji yayi yana mishi kallon babu abinda ban sani ba yace "Na sani, amma a labarin dana samu mutumin da zaka had'a ta dashi ba mutumin kirki bane, shiyasa ma na gabatar da d'ana dan shine ya dace da ita, tana son shi, shi ma kuma yana sonta, sab'anin waccen had'in da zakayi babu soyayya a cikinshi." Kawu Mamu da wannan karan kwarjinin Alhaji ne ya hana shi kallon idonshi, zufa ya ji ta fara tsatsafo mishi saboda tsoro da fad'uwar da gabanshi keyi, ganin yayi shiru yasa Alhaji cewa "Karka damu, ka fad'a mana duk abinda waccen ya biya ni zan ninka maka shi, sannan ka tsaga wa Zeituna sadakinta, a take anan zan biyashi." Da k'arfi ya kalleshi yana d'an nazartarshi, wata zuciyar ce ta nuna mishi karya saki reshe ya kama ganye, inda wata zuciyar ke nuna mishi ai ba k'ananan mutane bane, dan haka kamar sub'utar baki sai kuwa yace "Da gaske zaku biya ko nawa ne?" Lieutenant da yaji wata tambayar sakarci kallonshi yayi yace "A cikin mu nan akwai k'aramin yaro ne da za'a zauna ana maka karya? Ka fad'a kaga aiki da cikawa mana." Saida gaban kawu Mamu ya fad'i dan yanda ya mishi magana babu alamar arzik'i a ciki, Alhaji ya kalli yace "Shin zaku iya biyan waccen mutumin kud'in shi jaka d'ai-d'aya har jaka d'ari biyu?" Alhaji ne ya kalli lieutenant wanda ya d'auka ko shi zai biya kud'in, hannu yasa aljihu da niyyar fito da kud'in daya d'auko saboda baisan ina zasu zo ba Alhaji ya dakatar da shi ta hanyar fito da kud'i daga aljihunshi ya aje gaban kawu Mamu yana fad'in "Wannan jaka d'ari biyar ne, ka biya mutumin kud'in shi da duk wani abu da kasan ya wa yarinyar ko kuma kai, saura sadakinta?" Kawu Mamu jikinshi ne ya fara rawa hannayenshi na kakkarwa wajen d'aukar kud'in, mamaki yake ace masu kud'i basu d'auki kud'i a bakin komai ba, wai har riga rigan fito da kud'in suke ma, kenan kowanensu ya bawa jaka d'ari biyar baya? Ya d'auki kud'in yana ta zanzarin ya saka aljihu yaji Alhaji yace "Ka yanka mata sadaki mu biya." Kallonshi yayi duk ya rud'e yace "Alhaji ko nawa ma ku kawo, ai ku manyan mutane ne, Zeituna ta zama taku halak malak." Murmushi Alhaji yayi yace "Ka fad'a min sadakinta kawai na biya, domin kuwa akwai sharud'an da nake son gindaya maka bayan hakan daga yanzu har zuwa lokacin da amarya zata zama k'ark'sashin ikon d'ana." Da sauri lieutenant ya kalle shi, wai da gaske Alhaji yake aure zai mishi? To shi kuma meyasa duk yaran gidan nan sai shi Alhaji ya zab'a? Me zaiyi da wani aure yanzu? Auren kuma ma da budurwa wacce bata wuce sa'ar 'ya'yan dana rik'e a hannu na ba (Hamna, Amna)? Meyasa Alhaji zaiyi haka ba tare da shawara ta ba? Auren farko na mahaifiya, aure na biyu kuma na mahaifi, d'an kawar da kallonshi yayi a zuciyarshi ya furta "Ya Allah." Kawu Mamu ne yace "Alhaji zaka iya biyan sadakin Zeituna?" Kallonshi yayi yace "Saurara kaji, idan ka zana sadakinta ba wai yana nufin kai zakayi komai ba, mijinta nan da kanshi ne zai mata kayan d'aki da lefe da duk wani abunda ake wa kowace 'ya 'yar gata, dan haka sadakinta da zaka fad'a yanzu inhar zaka bi kamar yanda addini ya tsara ne, to fa zaka bawa yarinya kayanta ta mora kamar yanda ita ce da zaman auren ba kai ba, idan kuma zakayi yanda muka saba ne a al'adance, to shine zaka cinye ba tare da yarinyar ta gani ba, amma duk da haka karka manta wani abu, Zeituna zata shiga gidan da million dubu ma tafi k'arfin ta bare tsirarun kud'in sadakinta." A wannan karan kam yanda yaga shi kanshi Alhaji yayi magana sai al'amarin ya fara bashi tsoro, dan haka cikin rawar baki yace "Kawai ku bada jaka d'ari ma." Wani murmushi Alhaji yayi na takaicin abinda kawu Mamu ya fad'a, dan shi ya zo ne ya nuna mishi gaba da gabanta, ya so ya yanko kud'in da shi a ganinshi ya fad'i k'arshen kud'i shi kuma saiya ninka mishi, ba dan komai ba sai dan yasan darajar 'yar da kuma bin dokokin da zai gindaya masa, hannu yasa aljihu duka rigarshi ya fito da kud'i da suka fi na d'azu, aje mishi yayi gabanshi yace "Ka rik'e wannan sadakin Zeituna nena biya lakadan ba ajalan ba, ka saka mana ranar da zaka d'aura aure mu zo mu d'auki surukata, tsinke bana buk'ata daga gareka." Kawu Mamu fashewa yayi da kuka yana kallon kud'in yace "Alhaji, yanzu wannan kud'in nawa haka? Wannan ai ba zan iya irgasu ba, kona fara ba zan gama ba sai na kai shekara guda." Murmushi Alhaji yayi yace "Million d'aya da rabi ne, a hakan ma dan ka fad'i kad'an ne, na so na biya sadakin da zai zautar da kai ko ka shiga hankalinka, ka gane cewa 'ya'ya da Allah yake bamu ba dan mu wulak'antar da rayuwarsu bane musamman akan kud'i." Sam kawu Mamu hankalinshi bai kai ga tunanin abinda Alhaji ya fad'a masa ba, Alhaji ne yace "Yaushe ka saka ranar d'aurin auren?" Lieutenant ne ya mishi kallon mahaifina ka ceceni mana, kamar zaka gurgunta rayuwata ne fa, Alhaji kuma bai kula shi ba sai kawu da yace "Kawai ku zab'i ranar data muku sai a d'aura auren." Alhaji kuma dake son gaggawar d'auke Zeituna daga hannunshi ne yace "Idan na ce maka ranar juma'ar nan ban takura ka ba?" Kallonshi kawu Mamu yayi ya d'an fara lissafi kafin yace "Nan da kwana uku kenan?" Kai ya jinjina mishi dan haka yace "Ai kawai babu wata damuwa, babu takura ko kad'an, gobe ma da kaina zanje duk rugagenmu na sanar da sauran dangi dan su zo a shafa da su." Alhaji ne yace "Abu biyu zuwa uku nake son fad'a maka, daga yanzu har zuwa lokacin da Zeituna zata bar gidan nan ban yarda ta sake zuwa aiki ba, sannan daga yanzu bana so aiki ko na gidanka ne tayi komai k'ank'antar shi, sannan kada ta zama cikin takura ko matsi har lokacin da za'a d'aura auren nan, idan ka kiyaye wannan sai mu zauna lafiya da kai, ina fatan ka fahimta?" Mik'ewa Alhaji yayi lieutenant ma haka suka nufi mota kawu Mamu na fad'in ai za'a kiyaye, da haka suka shiga mota suka sake d'aukar hanyar komawa gida, sai lokacin ne Alhaji ya kalli lieutenant yace "Babba, nasan kana cike da mamakin abinda na aikata ko, kuma kana son sanin dalilin da yasa na aikata hakan, yarinyar nan tana cikin wani hali a gidan kawun nan nata, sam ba mutumin kirki bane tunda har zai iya karb'ar kud'i a hannun wani mutum ba dan ya aureta ba sai dan ya dinga lalata da ita ta duburarta, uk'ubar da suke saka yarinyar ma kad'ai bai isa ba shine harda neman ruguza rayuwarta, dalilin haka ta fara tunanin barin garin nan ko zata ji dad'i a ranta, domin kuwa ta kamu da son wani da bai ma san tana yi ba, ni kuma ina jin haka shiyasa nayi gaggawar d'aukar mataki tun kafin ta shiga uwa duniya." Jinjina kai lieutenant yayi yace "Kayi daidai Abba, amma maimakon ka had'a ta dani ai da wanda take so d'in ka had'a ta da shi, zata fi farin ciki a hakan amma bani ba, Abba na mata tsufa dayawa, ina da matata da yarana, bana da tunani ko niyyar k'ara aure, yarinyar! Abba a duba k'uruciyarta, kada a tauye ta saboda bata da gata." Kallonshi Alhaji yayi yace "Dan kana da mata da yara sai akace ba zaka k'ara aure ba? Ko kuma dan kai babu burin yin hakan a ranka sai kuma ubangiji ya barka haka? Duk kunbi kun d'orawa kanku rayuwar turawa saboda kawai kunsha boko kun k'oshi, Allah ya hore muku abinda zaku zauna da mace hud'u amma kuna mak'ale a mata d'aya d'aya, to ban lamunta , wannan karan k'addararka ta zo maka da sake k'ara aure bayan ka fara girma, kuma ta hanuna wannan k'addarar ta jefo auren naka, kayi na farko saboda uwarka, yanzu zakayi na biyu saboda ni ubanka, idan kuma ban isa ba na gani, wallahi ba kai ba har uwarku da kuka ga ina zubawa ido wannan karan sai mu samu matsala da ita akan auren nan." Lieutenant da gabanshi ke dukan uku uku yake takaicin musawa mahaifin nashi wanda sanadiyar haka yau gashi yana kallon fad'an shi da abune mai matuk'ar wuya ganin hakan tare da shi, cikin girmamawa yace "Dan Allah Abba kayi hak'uri ka gafarce ni, wallahi bana da tunanin bijirewa buk'atar ka, kawai yarinyar ce na duba, amma kayi hak'uri insha Allah ba zan baka kunya ba." Shiru Alhaji yayi ya kawar da kanshi suka ci gaba da tafiya, saida suka kusa daf da gidan ya juyo a nutse yace "Shin ka ma san yarinyar nan wa take so? Kasan waye ta jima tana dakon soyayyarshi a zuciyarta?" Kai ya girgiza shi kuma yace "Kai ne, kai ne wanda take so, kai ne kad'ai mutumin da zata iya zaman aure dashi tayi farin ciki, da kunne na naji tana fad'in haka wanda maganar daga zuciyarta take fitowa, babba kayi hak'uri idan na takura ka, sannan ka min biyayya ta hanyar nuna wa yarinyar nan soyayya da gata, zan so ace ta manta da maraicinta, ku har yanzu baku san meye maraici ba, baku d'and'an d'acin dake cikin maraici ba dan haka ba zaku fahimta ba har sai ranar da kuka wayi gari kuka ga bama raye a doron duniya, amma ina baka tabbaci akan yarinyar nan zakayi alfaharin wannan had'in dana maka." Jinjina kai yayi alamar gamsuwa a haka suka ci gaba da tafiya sannu sannu har suka iso gidan. *Tunda* Jibril ya je mayanka bai dawo ba saida tik'ek'en sa wanda Huda ta zayyana masa kamaninshi, a babbar mota aka saka shi wacce samanta ke bud'e shi kuma yana gaba dan jagorantarsu, suna zuwa har k'ofar gidan ya samu yaro ya aika yace a kira Mari, ta so fitowa da Huda amma tana can yau ta samu kayan mak'ulashe ko takan uwar bata bi ba, tana fitowa ta ganshi suka sake ido hud'u hud'u, rumgume hannayenta tayi a k'irji ta kalli san dake bayansu ta kalle shi tace "Sai gashi bayan shekara bakwai mun sake had'uwa, bawan Allah mena maka a rayuwa daka tarwatsa min tawa rayuwar? Laifin me na aikata maka daka zab'i hukunta ni ta hanyar raba ni da iyaye na? Kuskuren mane aikata a kanka daka gwammaci ka rama ta hanyar yi min ciki na haifi yarinyar da ake kiranta da shegiya? Meyasa? Ko fa saninka banyi ba a waccen ranar, amma ka kasa tuna komai ka zalince ni sannan ka tafiyarka ka barni da abun kunya, kai wane irin marar imani ne?" Tunda ta fara magana yayi k'asa da kanshi yana k'ok'arin b'oye hawayenshi, saida ta gama ya kalle ta yace "Kiyi hak'uri Ma..." Bata bari ya k'arasa ba ta gaure shi da Mari a gaban mutanen dake jiranshi ya fad'a musu yanda zasuyi da san nan, ko dafe kunci baiyi ba bai kuma nuna abun ya dame shi ba, dan yasan ya cancanci fiye da haka ma a wurin ta, cikin shak'ewar muryar da tasha kuka tace "Kai har kana da bakin da zaka bud'a ka bani hak'uri? To bari kaji da kyau, wallahi ba son auren d'an uwanka nake ba, amma zan aure shi saboda kai sannan na shiga da 'yata gidan ubanta, abinda zan fad'a maka kawai shine kada ka yarda wani ko wata ace za'a gorantawa 'yata cewa ita agola ce ko shegiya, wallahi duk wanda ya fad'i haka saina tona maka asiri, wannan shine dama, ka b'ace daga k'ofar gidan nan." Zata wuce ya tare gabanta yace "Dan Allah Mari ki saurare ni." Kallon da take masa kamar zata ci namansa d'anye dan haka yace "Ki dake ni mana idan hakan zai saki ki huce laifin dana miki, amma ina rok'onki ki bani dama na fara cikawa 'yata burinta ta hanyar yanka mata waccen sa a sake zana mata suna, ina so masu mata gorin ba'a yanka mata ragon suna ba su san 'yar gata ce ita ma." Wani kallon mamaki ta masa tace "Gata? Yar gata fa kace? Shin kasan wahalar da nasha da ita kanta Huda?" Had'e hannayenshi yayi yace "Dan Allah fa nace Mari, na rok'eki ki amince na faranta mata rai." Tab'e baki tayi tace "Ka amince da abinda na fad'a maka cewa ban yarda kowa ya zagar min 'ya ba? Sannan ka yarda zan je da ita gidanku ba'a matsayin agola ba?" Da sauri yace "Na amince Mari, babu ma wanda zai goranta mata." Sake tab'e baki tayi tace "Shikenan, sai kayi abinda ya dace." Juyawa tayi ta shiga ciki shi kuma yace yaran su d'an jira kad'an, yana rufe baki kuma sai kiran sallah la'asar, dan haka sukayi alwala suka shiga masallaci, ana idar da sallah yace akwai zanen suna na Huda wanda ba ayi ba a baya, nan fa aka sake rad'in suna kowa ya sake shaidawa ya bayar da kud'i aka siyo carton d'in alawa aka raba, wannan gabjejen San aka kayar aka yanka shi, daga nan shi kuma yace ya gama nashi burinshi yaga an zubar da jinin dama, nan fa nama aka dinga wadak'a da shi sai gashi har masu goranta mata sun manta suna wawasar nama ana sadaka, Iklima kam a tsakar gidan su habaici da zagi babu irin wanda bata aikawa matan gidan ba banda Mamar Husna, ana tsaka da haka motar da zata d'auki su Mari ta zo, ai kuwa Iklima tace k'afar ta k'afar Mari, tare suka d'auki hanya da Huda sai fatan sauka lafiya. *Bayan* fitarsu Alhaji ba jimawa Ammar ya shigo gidan har falon Hajia, wannan karan Ummy ce zaune da yan biyunta sun sakata tsakiya, amma daga wacce faranti ke kan k'afafun ta tana ta gwaigwayar kankana ma zaka fahimta, Hamna na gashinshi ta zabura ta aje farantin zata haura d'akin su, da k'arfi Ummy ta jawota ta zaunar da ita tace "Haukan banza, sau nawa zan ce miki ke ba yarinya bace ki daina sarar gudun nan." Ganin yayi tsaye yana mata wani kallo yasa Ummy had'e rai tace "Kai kuma lafiya? Meye ka wani tsaya mana a gaba haka?" Kallon Amna yayi yace "D'auki kisha." Girgiza kai tayi alamar toh ta sunkuya ta d'auki farantin da yer uwarta ta aje tasa kankanar gaba ta fara sha ba dan ranta na so ba, dan ita ko warinta bata cika so ba amma haka ta ke sha, Ummy ce ta kalleta tace "Ke da baki shan kankana shine zaki sha ki takura kanki, mtsss wallahi abun haushi baya k'are muku." Kallon Ummy yayi ya kalli kankana dake bayanta sai k'ara b'oyewa take ya matso, hannu ya kai zai kama kunnenta Ummy ta buge hannun tana fad'in "Wallahi ubanka zan ci idan ka tab'a min 'ya, wai kanka d'aya kuwa." Sake had'e rai yayi cikin jin zafin zagin data masa yace "Ki bari ki ga me zanyi, tarbiyar da kuka kasa mata ce zanyi mata." Da k'arfi tace "Tarbiyya? Kai tarbiyyar ce da kai da har zaka wa wani? Dallah malam fitar min anan wurin kafin ranka ya b'ace." K'asa yayi da hannunshi kamar zai kama kunnen Hamna hakan yasa Ummy yin k'asa da sauri da niyyar rik'e hannun, cikin azama ya saka d'aya hannu ta sama ya kama kunnenta ya murd'e, wata uwar k'ara ta saki a kunnen Ummy ta fashe da kuka tana k'amk'ame ta, k'ok'arin yakice hannun ta fara yi amma ina ta kasa, shi kuma Hamna data bud'e bakin nan yayi nasarar buga mata hannu dole tayi shiru ta rufe bakin da hannaye yana fad'in "Wallahi kashedi na k'arshe zan miki, idan kika yarda kika sake fita daga gidan nan babu hijabi sai na ci k'undun ubanki, kuma wallahi tun a inda na had'u dake zan fara bugaki har cikin gidan nan, tunda dai ba kya jin magana ke, munafuka kawai." Sakinta yayi ya juya ya bar d'akin Ummy ta bishi da bala'i amma ko a jikinshi, da fitarshi kuma sai ga colonel ya iso har cikin gidan yan rakiyarshi suka shiga, saida zai shiga d'aki ya dakatar da su ya shigo ciki, saida ya gaisa da mutane sosai da yara kafin ya shiga dan yin wanka. Ya gama wanka ya saka dogon wando da singlet zai saka riga Zeinabu sarkin tsegumi tace "Amma dai kasan duk cikin sabgar nan da za ayi mu akafi cuta ko?" Da mamaki ya juyo ya kalleta ya dakata da saka rigar yace "Me? Cuta fa kika ce? Cutar me aka mana?" Zaune tayi bakin gado tana fad'in "To kayi tunani mana ka gani, mu fa yara uku zamu aurar lokaci d'aya, kuma biyu daga ciki mata ne, ka kuma san auren mata yafi na maza kashin kud'i, kaga kywa ai zamu shiga uku." Kallon anya kuwa matar nan nada hankali ya mata? Dan shi dai inba hauka ke damunta ba baiga abun mita ba anan, da mamaki yace "Zeinabu yaushe kuma gidan nan muka fara rayuwar tsiya da talauci? Yanzu ke duk a lamarin nan kud'in da zaki kashe ne matsalarki? Ba wai farin ciki da 'ya'yanki zasuyi aure ba, meyasa kike hakane? Ke nama ji zamu kashe kud'in, babu kud'in ne na kashewa? Ko kuma ke aka ce ki fito dasu ki kashe bare ki wa mutane iya shege, sannan meyasa bakiyi tunanin d'an uwana ba da kuma matarshi Sa'ada? Su fa duka yayansu maza ne wanda su zasu kai, ke kuma d'an ki d'aya ne zai kai biyu kuma mata zasu kawo miki abun arzik'i, mtssss, wallahi Zeinabu matsalarki tayi yawa." Mik'ewa tayi jin k'orafinta yau ma bai karb'u ba ta nufi k'ofar fita tana magana k'asa k'asa da fad'in "Aikin banza, ai nasan dama ba tunani gareka ba bare ka hango abinda na hango mana, indai har zamuyi yanda akeyi ne ai mazan idan sun kawo mana sai mun kusa ninka musu abinda suka kawo a cikin gara." Tana daf da kaiwa k'ofar taja tsaki tare da murgud'a mishi baki, da k'arfi ya juyo dan tabbatar da gaske ne abinda yaji wai, ita ma sai bayan tsakin ya fito ta fahimci bala'in data jawowa kanta, ai da wani irin k'arfi yayo kanta zai cabkota amma hukuncin ubanjigi saita zame ta juya da gudu ta fad'a ban d'aki duk da k'ok'arin shi na son cabkota, tana shiga da iya k'arfinta ta maido k'ofar ta rufe daidai yana kawowa, kile tasa ta rufe gam shi kuma ya shiga bubbuga k'ofar yana fad'in "Zeinabu ni? Ni kike wa tsaki! Zeinabu yaushe kika raina ni haka? Allah ki bud'e k'ofar nan ko na karyata." Wata irin jijjiga ya wa k'ofar da yasa ta fara motsi da k'arfi kamar zata karye, Zeinabu kam ciki ya d'uri ruwa sosai, tasan inhar ya bud'e to saiya karyata kam, yana cikin jijjiga k'ofar da k'arfi Sa'ada da tun farkon fara bubbuga k'ofar shi taji dan tana falon zaune ta kira Junaid tace ya zo, yana zuwa d'akin ya bud'a ya shigo da sauri ya tunkaroshi ya rik'e shi yana fad'in "Yi hak'uri dan Allah Abba, kayi hak'uri, muje ka rabu da ita." Wani kallo ya ma Junaid ido jawur ya fizge ya shak'i wuyan rigarshi yana fad'in "Dan ubanka waya kawo ka? Me ma ya shigo da kai? Ka zo ne ka shigar ma uwarka? To yau saina kasheta a gidan nan, nace saina kasheta idan ya so nima a kashe ni." Yanzu kam Junaid ya fahimci uwar tashi ta kwanto musu kura, turashi yayi ya kaiwa bango karo ya sake kama murfin k'ofar ya jijjiga da k'arfi, cikin d'aga murya yace "Shikenan, ai kin k'i bud'ewa ko, to bari kiga yanda zanyi da k'ofar." Da sauri ya juya kayanshi daya shigo dasu ya fitar 'yar k'aramar bindigar dake jikin kayan ya zaro ya nufo k'ofar, Junaid na ganin haka ya shiga gaban k'ofar yana sake bashi hak'uri amma saiya ture shi gefe, ganin abun yafi k'arfin shi yasa shi fitowa yayi daidai da fitowar Hajia, da sauri yace "Hajia dan Allah ki zo kafin Abba ya kashe Umma, wallahi ranshi ya b'ace." Da azama ta tako ta shigo d'akin tana fad'in "Kisan kai? Karfa yaran nan ya ja mana masifa a gida." Tana shigowa daidai colonel yasa k'afa da k'arfi ya bangaje k'ofar, Zeinabu na jin ya bud'e ta dafe kanta da hannaye ta k'ame wuri d'aya ta rintse ido jin fitsari na zubo mata daga tsaye, shi ma kuma yana ganinta gabanshi ya saita bindigarshi ya nuna mata yana fad'in "Me na fad'a miki? Bance miki ki bud'e ba kafin na shigo da kaina, to yau zzzz..." Bai k'arasa ba Hajia ta shiga tsakaninsu tace "Ka kashe ni Hussein kafin ka kasheta, tunda so kake ka jawo mana abun kunya." Ganin Hajia gabanshi ya sa shi kaucewa cikin hassala ya buga bindigar a bango ya saketa ta fad'i shi ma kuma ya kaiwa bangon duka da hannunshi, a hankali Hajia ta dafa kafad'ar shi ta shafa, shiru yayi bai juyo ba hakan yasa ta kama hannunshi suka fita zuwa falo, Junaid kuma kallon mahaifiyarshi yayi cikin ladabi yace "Umma dan Allah ki rage duk wani abunda kika san Abba baya so, duk zafin zuciyar Abba kana iya zama kayi hira da shi ku fahimci junanku, amma ko yau Abba zai shigo gari sai kaji hayanuyarshi kin b'ata masa rai." Haushi ne yasa Zeinabu cewa "Kai ni fita ka bani wuri, tunda kana bayan uban naka saika zo ka bashi kashi." Tsaki tayi ta mayar da k'ofar ta rufe duk da bata rufu da kyau ba dan ya riga ya b'allata, shi kuma fita yayi ya samu mahaifin nashi zaune ya tangale gwiwoyin hannunshi kan cinyoyinshi ya dunk'ule hannunshi yana dukan d'aya hannun, Hajia ce kawai zaune tana kallon tv da tunanin idan ya sauko sunyi maganar da zasuyi akan tafiyarsu ta gobe, suna haka su Alhaji suka shigo tare da lieutenant, bai ma kowa magana ba kuma suma basu damu ba sun san kayan ne suka motsa, zaune sukayi sai Alhaji daya kalli Junaid yace "Ka kira min uwar 'yan biyu, idan ka dawo ka kira min su kansu yan biyun." Sama ya haura ya samu Sa'ada can ya kirata ya dawo, b'angaren su ya nufa ya kira Ammar da Amar suma suka zo, Alhaji da kanshi ya kira Husseina da Labaran da suke tattaunawa suma kan auren Jibril da Jamila, saida suka had'u ya kalli kowa da kyau kafin yace "... 👏👏👏 17/06/2020 à 22:08 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _19_ "Abinda yasa na taraku dama dan na fad'a muku wani abun alkairi ne daya tunkaro mu, insha Allah nan da kwana uku zamu sake yawa a gidan nan." Shiru kowa yayi sai kallonshi da suke babu wanda yace wani abu, Husseina ce tace "Masha Allah, ah lallai abun farin ciki tunda zamu k'aru ne, amma ta ina?" Kallon Hajia yayi data tsura mishi ido tana jiran tajiba daidai ba ta fara masifa, had'e rai yayi sosai dan karta kawo mishi wasa kafin ya kalli Sa'ada yace "Sa'ada, kiyi hak'uri abisa abinda ya faru, laifina ne bana mijinki ba, kamar yanda zaki ji yanzu shima haka kawai yaji na yanke hukuncin, amma na tabbata idan kuka ji dalili na zaku fahimce ni, nasan kina da ilimi kuma ba yarinya bace ke, idan har kin kama girmanki hak'ik'a zakiji dad'i sosai anan gaba, 'ya na d'auke ki kamar yanda babba yake d'ana, ina fatan kema zaki min biyayya." A ladabce ta kalleshi ta kashe murya tace "Abba insha Allahu ba zan baka kunya ba, nima a uba nake kallonka wallahi, ka isa ka zartar da kowane irin hukunci a kanmu bamu da ja akai." Cikin jin dad'i yace "Alhamdulillah, nagode da kika fad'i haka, dama ba wani abu bane, yarinyar nan dake muku aiki Zeituna, ita ce a wani mawuyaci hali da tale buk'atar taimako, shiyasa yau d'in nan na nemawa *Baba na* aurenta, kuma kawunta ya amince nan da kwana uku za'a d'aura auren bayan sallah juma'a insha Allahu." Kowa kallonshi ya sake yi, kusan tambayoyin d'aya ne suke yawo a zuk'atansu, Zeituna? Lieutenant kuma? Meyasa sai shi to? Wani murmushi Sa'ada ta k'irk'iro tace "Masha Allah, Abba wannan abun farin ciki ne daya kamata mu godewa Allah, gaskiya naji dad'i har raina wallahi, Allah yasa alkairi ya bamu zaman lafiya, gata kuwa yarinya mai nutsuwa da ladabi, dan ko ido bata had'awa dani." Kamar daga sama Ammar dake zaune k'afa d'aya kan d'aya yana danna waya yace " Amma ai tana had'awa da mijinki ko? Kinga Ummy karki fad'i abinda kika san ba haka bane, mu maza munfi kowa sanin yanda kuka tsani kishiya kamar yanda kuka tsani mutuwarku." Kallonshi kowa yayi amma shi hankalinshi na kan waya bare ma ya ga kallon da bai masa ba ya sake magana, Husseina ce tace "Amma Ammar ai sai mu jinjina mata tunda har zata iya k'ok'arin b'oyewar ma." Sai lokacin ya d'ago ya kalli lieutenant ya kalli Alhaji yace "Alhaji, yanzu domin Allah meyasa sai Abba zaka had'a ta dashi? Shin kaga yarinyar kuwa? Ita fa yarinya ce shi kuma tsoho, me zai sa idan taimakonta kake so kayi ka k'i had'a ta da d'aya daga cikin matasa majiya k'arfi? Amma ace sai uwar mu ce kawai ake sha'awar ganinta da kishiya, to gaskiya ni dai ban amince da auren nan ba, ai ga Jamil nan, ya isa aure shima, a had'a shi da ita ma tunda shine Hajiar makka bata wa mata ba, idan yarintar shi kuke gani ku had'a shi da ita nan da kwana ukun kuga idan ba'a nuna muku bayyanar ciki gwajin da za ayi mata fa kafin bikinmu, dan haka kawai ku bar maganar nan." Lieutenant ne ya kalle shi yace " To marar kunya fitsararre, kenan duk wurin nan kai kafi uban kowa bakin iya magana, wai ni wa ma ya gayyato shi wurin nan ne da har zai zo yana mata iya shege?" Gyara zama Ammar yayi yace "Ni fa ina zamana aka ce na zo, kasan meyasa aka ce na zo? Saboda nine babban d'an ka kuma sanyin idaniyarka na farko, ana so aji ta bakina ne kuma na fad'a ni dai ban yarda a had'a k'azamar yarinyar nan kishi da uwata ba." Lieutenant zaiyi magana Alhaji ya kalli Ammar yace "Ammar wannan fa hukuncin dana yanke ne, yanzu ja zakayi da ni kenan? Bayan shi kanshi uban naka ya amince." Mik'ewa yayi yace "Da alama ba zamu fuskanci juna daku ba, amma yarinyar nan tana shigowa gidan nan a matsayin matar ubana kuma kishiyar uwata wallahi saina rabata da mak'ogwaronta in yaso ayi duk wacce za ayi." Colonel da har yanzu Zeinabu yake hangowa shi dai kallon kowa kawai yake, juyawa Ammar yayi zai fita Hajia wacce farkon al'amarin ita ma daru taso tayi, amma ganin babban jikan nata ya nuna bai yarda ba alhalin gata zaune yasa ta shirya b'ata mishi rai, cikin gadara tace "Ka ce baka yarda ba? To yanda da baka yardan ba ya za ayi kenan? A fasa?" Juyowa yayi yace "Eh haka nake nufi." Murmushi ta masa tace "To bari kaji Ammar, wallahi auren nan kamar anyi an gama, yar aikin gidanku zata shigo gidan nan a matsayin kishiyar uwarka, za'a ware mata d'aki kamar yanda aka ware ma uwarka, ubanka zai raba musu kwana, a gaban idonka dana uwarka zai shiga d'akin amaryar shi sai dai in kunga haka ku had'e zuciya ku mutu, kai idan da rabo ma nan da wata tara sai kunga sabon k'anenku da idonki." _Ina fatan dai kun fahimci inda yayi gadon rashin kunyarshi da fitsara?_ Wata dariyar rashin mutumci ya mata yace "Hajajju mutan makka, ban miki musu ba cewa madarar mahaifina zata iya tasar d'an adam ba, amma gamsar da ita matar kam w..." Cak ya tsaya da kalamanshi saboda saukar marin akan kumatunshi, Ummy ce tsaye gabanshi tana huci dan ba zata iya saurarenshi ba, da yatsa ta nuna masa k'ofar fita tana fad'in "Fita daga d'akin nan, ka fita nace." Kallon Ummy yayi idonshi jawur da su kamar zai kama da wuta, cikin wani irin yanayi ya kalli Ummy kai kace ramawa zaiyi yace "Ummy mari na fa kikayi? Akan maganar k'azamar yarinyar da tsabar datti da za'a d'auke ta a jefa a cikin ruwan *Madarunfa* babu abinda zai hana ruwan yin bak'i k'irin, shikenan na fita." Kallon Alhaji yayi wanda shi kanshi baiji dad'in marin ba yace "Alhaji na zo ne saboda ance kai kake nema na, amma ba dan haka ba da babu abinda zai sa na zo dan duk nan ciki bayan kai babu wanda zai iya kirana domin magana ta arzik'i." Juyawa yayi zai fita cikin k'arajin murya Ummy ta fashe da kuka tace "Fita d'an iska kawai, duk nan ciki waye sa'anka da zaka zauna kanawa fitsara da rashin kunya." Tsayawa yayi ya juyo da k'arfi da niyyar magana amma kuma zuciyarshi bugawa take da sauri, k'urawa Ummy ido kawai yayi kamar zai cinyeta d'anya, bubbuga k'irjin ta tayi tace "Eh na fad'a, kai sarkin zuciya ko? Ranka ya b'ace ne? To zo ka dake ni Ammar." Husseina ce ta mik'e ta kamata ta zaunar da ita tana fad'in "Dan Allah Sa'ada ki daina zubar da hawaye akan d'an da kika haifa a cikinki, shin kinsan tasirin da hakan zai masa kuwa?" Cikin kuka ta kalli Husseina tace "Hajia menayi? Wane laifi na aikata a duniya dana cancanci haihuwar Ammar? Shi fa ba k'aramin yaro bane, amma kullum saiya b'ata min rai a gidan nan hankalinshi ke kwantawa." Ammar da har yanzu ke tsaye yana kallonta idonshi ne suka sake rinewa, bugun zuciyarshi kuma ya sake nunkuwa, had'e hannunshi yayi ya dunk'ule shi cikin b'acin rai da neman wanda zaiyi masifa da shi ya juya, ai kuwa tvn Hajia ya kalla ya gabzawa dunk'ulellen hannun nan, abinka ga tvn zamani kuwa wacce ke manne a jikin bango sai kuwa ta gabce ta fad'o k'asa inda ta bugi k'aramin teburin glishin da aka d'ora décoder da kuma remonte, a tare kayan duk suka fad'o suka watse, juyowa yayi lokacin da wasu hawayen bak'in ciki da takaici suka zubo daga idonshi cikin muryar da zata tashi hankalin mai sauraro ya rik'e murfin k'ofa yace "Idan har kun tsane ni ku kashe ni mana, me ma yasa kika bari na zo duniya baku kashe ni ba? Ku kashe ni mana na huta kuma ku huta, naji ni d'an iska ne, fitsararre, marar kunya, bana da anfani a gareku, baku ga anfanin haihuwata ba, to na mutu mana ina ruwanku?" Idan ka cire Hajia da lieutenant dukansu mutanen wurin mik'ewa sukayi tsaye saboda tsoron ganin halin da yake ciki, k'ofar daya rik'e sosai ya turata da k'arfi ta bada wata k'ara mai k'arfi, juyawa yayi kamar zai tashi sama ya bar d'akin ya nufi b'angarensu, Amar da d'an sauri ya fito da niyyar bin bayanshi Hajia tace "Shalele rabu da shi, ai dai kasan zuciyar ce ta motsa ko? Kuma kafi kowa sanin cewa yana hucewa kan wanda ma bai ji ba bai gani ba, dan haka rabu da shi karya illatala, ka barshi har ya sauko zai zo ya biyani tvn nan daya fasa bak'in munafiki kawai, dama yana jin haushin kallon da nake." Lieutenant ne yace "Rabu da shi, ba mai kai ba kar wanda ya kuskura ya tanka masa har zuwa lokacin da zai sauko." Alhaji dake tsaye ne cike da nuna rashin jin dad'i yace " Dan Allah magana mai dad'i ta dinga fitowa daga bakinku zuwa kanshi, ba kusan komai k'aramtar kalma kuka fad'eta tasiri take akan yaranku ba, kuma ya kamata ace kuna hak'uri dashi, yanzu nan kunsan dan kwana uku ba zai kula kowa ba." D'an k'aramin tsaki yayi ya nufi d'akin shi inda Hajia ta bishi da harara da gunaguni kuma daga lieutenant har colonel babu wanda bai gani ba, duk da hakan bai musu dad'i ba amma hak'ura sukayi, Sa'ada ma da sauri ta tashi ta shiga d'akin ta tana ci gaba da kuka inda lieutenant ya bi bayanta, Hajia ma mik'ewa tayi ta nufi d'akin Alhaji dan suyi magana, hakan ne ya bawa Amar damar fita ya bi bayan d'an uwanshi da tunanin shi kawai ke kan hannunshi daya rotse yake zubar jini amma shi yaga bai ma damu ba, colonel kuma kallon Junaid yayi wanda shi dama tunda aka fara magana tsaye yake yace "Saika wuce ka d'auko min rigata d'aki, dan inhar zan shiga babu abinda zai hana ni gota uwar nan taka." Da sauri Junaid ya juya ya shiga d'akin, akan gado ya d'auko rigar ya fito har lokacin Zeinabu na ban d'aki, yana kawo masa ya saka fita yayi ya bar gidan shima. Yana shiga kai tsaye d'akin magungunanshi ya shiga, zaune yayi akan gadon marasa lafiya dake tsakiyar d'akin ya duk'ar da kai k'asa ya rik'e hannun dake fitar jini, har yanzu ya kasa tsayar da hawayen dake zubo mishi, tafarfasa kawai zuciyarshi keyi na k'una da k'unci, iyayen da suka haife ni, amma kullum babu kalma mai dad'i tsakani na dasu, tun ina yaro na fahimci me kalmar d'an iska take nufi, menayi da suka tsaneni tun ina yaron da bansan daidai da rashin daidai ba? Mena aikata gare su haka dayasa suka k'ini? Shin na zo musu ba yanda suka so bane? Ko kuma guda suka so haihuwa sai ni na fara fad'owa duniyar? Ko kuma dai ni wani sirri ne tare dani da yasa kowa na gidan nan ya tsane ni? Menene shi? Wa zai fad'a min dalilin tsanar da suka min? Iyaye na su hantare ni, kakanta ta zageni ta koreni daga wajenta, da irin haka suka raine ni a gidan nan, babu wanda ya tab'a rarrashi na, babu wanda ya tab'a tambayata damuwa ta ko matsalata, akan me? Akan me! Ya fad'a da k'arfi har da saka k'afa ya ture doguwar kujerar dake gaban gadon saida tayi baya. Saukowa yayi ya d'auki alcohol ya bud'e ya rintse ido sosai ya dararawa hannun, wani rad'ad'i ne ya ziyarce shi amma a hankali ya bud'a ido ya kalli hannun yace "Wannan rad'ad'in bai kai rabin wanda nake ji a zuciyata ba a duk sanda suka kira ni da d'an iska." Wasu hawaye ne suka sake taho mishi hakan yasa shi fad'awa kan gadon ya zaune yasa bandeji yana laulaye hannun yana fad'in "Kuna kirana d'an iska a kullum, shin baku tunanin na zama d'an iskan ? Namiji ne fa ni, ina da sha'awa da son jin dad'i, ba kwa tunanin tasirin addu'arku wata rana ya kaini ga aikata b'arna? Idan haka ta faru shima saik ku sake kirana d'an iska?" Amar na tsaye k'ofar d'akin ya gagara shiga, yasan halin kayanshi ba zai tab'a bari ya rarrashe shi ba, abinda yaji kuma sai yaji kawai bari ya bashi wuri ya fad'i abinda ke ranshi ko yaji sauk'i, dan haka ya bar wurin cike da tausayin d'an uwanshi da kuma jin lallai iyayensu basa kyautawa. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Suna tafiya kawu Mamu ya tattaro kud'i ya shigo gidan afujajen kamar wanda zaho ya koro ya shiga bukkarshi, kud'in ya aje ya fito yana k'wala kiran Zeituna, ita ko tana can wajen yan bisashen da ake kiwo a gidan tana d'aure su, da sauri ta zo ta sunkuya gabanshi cikin fulatanci tace "Kawu gani." Shima a fulatanci yace "Me kikeyi?" Kallonshi tayi tace "Ina d'aure bisashe ne." Juyawa yayi ya kalli Jumma dake cin tuwo yace "Innar Jumare, daga yau Zeituna karta sake aikin komai a gidan nan, ko da d'auke kara ne daga nan zuwa can, aikinta a gidan nan karya wuce yin wanka ta ci abinci ta zauna ta huta, kinji ko? Har wurin aiki ma surukinta yace karta koma zuwa." Ya fad'a yana kama kunnenshi alamar taji, shek'ek'e Jumma ta kalleshi cikin k'warewa a harshenta tace "To me kenen zatayi idan batayi aiki ba? Ko mu bayinta ne da zamu dinga mata bauta?" Cikin d'aga murya yace "To sai me idan kun mata bautar? Ku shekara nawa ta d'auka tana muku bautar? Ke bari kiji wallahi, tuwon ma idan har tana buk'ata a saka mata shi a baki to sai an saka mata ko da hakan na nufin zan biya kud'in hakan ne, idan kuma kika bari na kamata a gidan nan kin sakata aiki, to wallahi zan iya sakinki saki har uku, in yaso in auro yar birni ke kuma ki koma rigarku." Kallonshi tayi tace "To wai meya faru ne? Akan me zaka ce zaka sakeni akan wannan mayyar yarinyar?" Cikin karsashi yace "Saboda aure zan mata nan da kwana uku, yarinya mai k'ashin arzik'i ce, yau ma daga babban gidan da take aiki ne aka zo neman aurenta." Tunda ya ambaci aure Zeituna gabanta ya fad'i ta d'aga kai ta kalleshi tace "Aure kuma kawu?" Yanda yaga firgici tare da ita yasa yace "Ke kwantar da hankalinki, ba zan had'a ki da wanda ba kya so ba, zab'inki ne zan had'a ko da shi wanda yake sonki kuma kike son shi, ni ban damu da tsufanshi ba tunda dai kina son shi." Kalamanshi sun k'ara sakata a duhun kai, Jumma kuma cewa tayi "Hum! Ayi dai mu gani Baffan Jumare, wurin son kud'in ka saika kaita inda za'a halakata." Da k'arfi yace "To ba bakinki ba, yarinya dai mai goshi ce wallahi, ke kinma san waye zai aureta? To Alhaji Hassan ne, babban d'an Alhaji Suley Gaga, nan gaba kad'an nima zakiji na zama Alhaji." Zeituna tsaye ta mik'e ta dafe k'irji tace "Kawu lieutenant?" Kallonta kawu yayi yace "Ke ba lantanan ba nace Hassan, tare da babanshi suka zo suka nemi aurenki, ke har ma na amshi sadakinki mun tsayar da ranar juma'a za'a d'aura auren." Sam ta kasa fahimta komai a zancen, lieutenant kuma? Ya zo neman aurenta? Anya kuwa! Me yake shirin sake faruwa kuma? Jin tana neman fad'uwa a wurin yasa ta juya ta shiga bukkarsu, Jumma kam dariya ta dinga yi tana fad'in "Ikon Allah, yanzu kuma abun ga tsoho ya kuma? To Allah ya kyauta maka." K'wafa yayi irinta haba dai zaki gama dariyarki ne idan kika ga na shigo gari nima, juyawa yayi ya bar gidan shima zuciyarshi fes saboda yana da kud'i aje a d'aki, sam ya manta da maganar wani Jano, yau ma Zeituna yanda taga safiyar nan haka taga wannan dare bata rintsa ba, tambayoyi ne birjik a ranta amma babu mai amsawa, gashi ma ance kar taje wurin aiki bare tasan abinda ke faruwa, ta rasa me zatayi da jin labarin nan, farin ciki? To akan me domin kuwa bata da tabbas, har yanzu gani take mafarki take ko kuma kawunta ne ya shiga shuhuba, bak'in ciki? To shima akan me? Da haka har asuba tayi mata bata rintsa ba saida tayi sallah bacci ya d'auke ta. *Washe gari* sammako sosai Ammar yayi ya tafi d'aurin auren Abdullahi, ana idar da d'aurin auren kuma ya d'auki hanya sai Madarunfa, awa d'aya ta kaishi a hakan ma dan baya gudu sosai ne, kamar haifaffen garin haka ya ratsa har ya isa gidan daya saba zuwa, paka motar yayi kai tsaye kuma ya shiga gidan yana sallama, matar dake k'ulla ruwa zaune bakin panpo ta amsa da farin ciki dan ta gane ko waye, mik'ewa tayi ta nufi wajen kujera ta d'auko tana fad'in "Ammar yau kaine da safiya haka? Amma dai sammako kayi sosai?" Murmushi yayi ya k'arasa yana karb'an kujerar data d'auko ya aje ya zauna yana fad'in "Aunty daga wurin d'aurin aure ne kawai na wuce." Zaune tayi kan kujerar data tashi ta kalleshi tace "Ina kwana." Bai amsa ba shima yace da ita "Ina kwana aunty." Sosai suka gaisa kafin ta sake mik'ewa ta bud'a fridge d'in dake cikin runfa ta sana'arta ta d'auko ruwa da lemu, kawo masa tayi ta aje ta juya ta d'auko faranti ta azo kwanonin abinci da duk abinda ya dace ta zo ta aje, saida ta zauna ta kalleshi tace "Ammar ga abinci ko, nasan dai ba lallai ka karya ka fito ba." Kallon dattijuwar yayi cike da k'aunarta, hak'ik'a yana son mahaifiyar su Hamna, baiji dad'in rabuwarsu da kawunshi ba amma k'addara ce, ita kad'ai ce suke fahimtar junansu kuma harya fad'a mata wani abinda ya shafe shi, tun yana yaro idan an hattareshi ia ke tarairayarshi tana bashi hak'uri, shiyasa har yanzu bai manta da ita ba duk da tana gidan wani amma yana ziyartar lokaci lokaci, wani lokacin ma idan ranshi ya b'ace ne ko kanshi yayi zafi yake zuwa ta bashi shawara da rarrashinshi, bai mata musu ba domin kuwa kamar gida ya d'auki nan, har mijinta zai iya yin hira dashi hirar da bata tab'a shiga tsakaninshi da mahaifinshi ba, da kanshi ya zuba abinci yana ci suna hira ta duniya harya gama. Su colonel ma sammako sukayi zuwa Goure, kuma cikin hukuncin ubangiji suka isa da wuri kai tsaye gidan suka nufa dan tare suke da Junaid da kuma Labaran, gidansu Maryama sun sha tarba sosai, kamar dai tarba da ita kanta Maryama ta gani zuwansu jiya tare da 'yarta da k'awarta, nan suka k'arasa gidan malam Rabi'u inda dama ansan da zuwansu domin su gabatar da abinda ya kawosu, suna zuwa can ma tarba suka samu inda suka samu maza uku bayan malam Rabi'u, tunda Labaran ya kalli tsohon yaji fad'uwar gaban da bai tab'a jin irinshi ba, haka suka zauna suka sake gaisawa sannan malam Rabi'u yace "... 👏👏👏 22/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _11_ "Nasan zaka gane muryata cikin sauk'i, dan haka ba zan bawa kaina wahala wajen sanar da kai wacece ba." Jin Sameera a bayanshi yasa shi juyawa ya kalleta wacce ita ma ke kallonshi saboda son sanin abinda ke faruwa, matsawa yayi sosai nesa da ita amma ita da bata fahimta ba saida ta sake bin bayanshi, domin kuwa jikinta na bata wannan wayar nada nasaba da halin da mijinta ke ciki, ganin bata daina biyarshi ba yasa shi fita daga falon ya rufe k'ofa, yana fita yace "Meyasa kika kira ni?" Murmushi tayi wanda saida yaji sautinsa kafin tace "Jiya mun rabu babu sallama baka kuma biyani kud'in aikina ba, shiyasa na kira dan na tuna maka karka manta da kud'i na." A k'ufule yace "Karki raina min wayo Nasmat, kiyi gaggawar sanar dani abinda yasa kika kirani, idan kuma dan wannan maganar ne to kiji da kyau, karki sake gigin kiran wayata, idan kuma ba haka ba wallahi zansa rayuwarki a had'arin da kaf danginki sai sunyi nadamar kasancewarsu yan uwa a gareki." Wata dariya tayi tace "K'arfin halinka na birgeni sosai, amma naga alama ba zaka saurare ni, shiyasa ma na tura maka da muhimmin sak'o a WhatsApp d'inka, zaka iya dubawa saika kirani muyi magana idan har kana son tsira da mutuncinka dana iyalinka." Kashe wayar tayi inda shi kuma cikin rawar jiki ya fara dubawa WhatsApp d'in, yana bud'e vidéon nan saida ya saki wayar bai sani ba tsabar firgita, da sauri ya sunkuya ya d'auki wayar ya sake kallon abinda ke ciki, take yaji jikinshi ya d'auki rawa, ya ilahi! Meyasa banyi tunanin haka ba? Ita ce tambayar daya wa kansa, da sauri ya nemi lambarta ya kira tana d'auka yace "Me kike so?" A tak'aice tace "Kud'i, kasan ku masu kud'in nan ba kwa tunanin talakawa da gajiyayyu, duk da kai kana k'ok'ari, to amma kasan dambu idan yayi yawa baya jin mai, kuma karka d'auka talauci ne yasa nayi abinda nayi." Cike da k'aguwa yace "Ki gaggauta fad'a min nawa kike so bana da lokacin b'atawa a tare dake." Cike da iko tace "Maganar nan ba zata yiwu a waya ba, mu had'u kawai." "A ina?" Cewa tayi "Ni ko a titi zan iya had'uwa da kai, bansan ba kai." Cikin jin haushi yace "Ba zan iya had'uwa da karya irinki a titi ba, zan turo miki da adresse d'in guest house d'ina ki sameni acan." Dariya tayi tace "Zan so duk inda zaka gayyace ni domin kuwa wannan videon ya shiga hannun d'an uwana." Tsaki kawai yayi ya kashe wayar ya tura mata adresse d'in ya shiga motarshi, hangen motarshi da tayi yasa ta fitowa da sauri tana so tayi magana, cike da damuwa ta bishi da kallo tace "Ya Allah, meke damunshi ne?" Saida yayi jiran minti kusan ashirin kafin ta iso, tana k'wank'wasa k'ofar yayi gaggawar bud'ewa ta shigo, kallon juna sukayi inda yaji zuciyarshi na raya mishi kamar ya mata dukan mutuwa, tana shirin zama yace "Fad'a min nawa kike so na baki da zaisa ki goge wannan d'aukar ba'a iya wayarki kad'ai ba har da k'wak'walwarki ma?" Tsayawa tayi daga shirin zaman ta kalleshi tace "Ko gaisawa ma ba zaka bari muyi ba?" A fusace yace "Bana ciki da shirme, karki b'ata min lokaci ke nake sauraro." Tsaye tayi da kyau tana kallonshi tace "Ina buk'atar naira million arba'in, yau ba sai gobe ba." Da k'arfi yace "What!" Matsowa yayi daf da ita ya galleta da wani mari saida ta fad'a kan kujerar da tayi niyyar zama ya nuna kanshi yace "Yanzu dama akan naira million arba'in ne kika sa na aikata zina? Akan wannan banzan kud'in kika saka na aikata abinda ban tab'a aikatawa ba tsawon rayuwa ta? Naira million arba'in kike so kika kasa fitowa ki fad'a min na baki? Nasmat kin cutar dani da rayuwata, ba zan tab'a yafe miki ba har abada." Mik'ewa tayi tana share hawayen wahalar da suka zubo mata tayi murmushin mugunta tace "Naji, ka tura min kud'in a wannan account d'in yanzu, ba zaka sake gani ba." Fizgar takardar data mik'o mishi yayi ya nuna mata k'ofa yace "Get out." Murmushi ta sake mishi ta nufi k'ofa, saida ta bud'e k'ofar zata fita ta juyo da murmushi tace "Mahaifiyata, tana gaisheka, baka canza a yanda muka sanka ba, saidai ka k'ara zafi sosai, kayi sukuwa akan mahaifiyata kamar doki tun zamanin k'uruciya, yau gashi 'yar daka raina kamar 'yar daka haifa a cikinka ita ma kayi sukuwa akanta, a gaskiya da zan samu namiji kamarka da zanji dad'in rayuwa dashi, dan ka zo min a yanda nake son namiji ya kasance min, see u *Dady*." Tunda ta fara maganar nan kanshi ya fara wani bala'in nauyi, mahaifiyarta, yar daya raina kamar yarsa, wa kenan? Yar daya raina har ya mata aure ita ce *Husna* yayarsu Abdul, to amma ai ba komai tsakaninshi da mahaifiyarsu Safeena, sai dai ko... Cak yaji tunaninshi ya tsaya kanshi ya kulle, sunan da zuciyarshi ta ambata ne yayi barazanar tafiya da numfashinshi, da k'yar ya iya had'a sunan Sss... al..m...a, k'ara waro ido yayi yace "Kenan Ma'arufa ce? Na shiga uku ni Abbas mena aikata haka?" Ya d'an jima a wannan halin yana tunanin da sam babu mafita, yana cikin haka yaji wani sak'on ya shigo wayarshi, da sauri ya duba dan a tsorace yake, yana dubawa kuma me zai gani? Sabuwar lamba ce ta turo mishi hotunan Raihan tsirara, zunbur ya tashi tsaye ya rufe ido ya dafe kanshi yana so ya samu kowace irin addu'a a baki amma ya kasa, a karo na biyu sake sakin wayarshi yayi ya fad'i kan lallausan carpet d'in, voice not d'in da aka turo ne yayi saurin d'auka ya bud'e, tattausar muryar Saleem ce yace "Shin da kake nan zaune gida ka tura 'yarka can kasan me take aikatawa ne? To wannan ma sanfuri ne, nan gaba zan turo maka da video yanda nake mu'amulantar ta." Cikin matsanancin sauri ya nemi lambar Raihan, tana d'auka daga can b'angaren cikin muryar dake son yin kuka yace "Kiyi gaggawa ki shirya kije airport, ki hau duk jirgin da kika samu ki dawo gida *Raihan*." Tabbas Raihan ta tsorata dan kuwa bata tab'a jin ya kama sunanta ba, cikin sauri kamar yanda yace ta tattaro kayanta ta nufi airport d'in, tayi sa'ar samun jirgin da zai tashi zuwa Abuja, dan haka ta hau aka juyo da ita babu shiri. Suna gama yawa ya sake yin zaune yana matsa k'irjin shi da yaji ya mishi bala'in zafi, tunanin abinyi yake nema har saida yaji lambar nan ta sake turo mishi da sak'o kamar haka _"Kayi gaggawar aurar da ita, idan ba haka ba zan kafa mata tarihi kuma mummuna, idan bakayi abinda nace ba wannan hotunan zasuje inda baka tsammani ne, domin kuwa zan d'ora su a kafafen yanar gizo ta yanda kowa zaiga tsiraicin 'yarka, a haka ma zata rasa mijin da kuka zab'a mata."_ Had'a kanshi yayi da gwiwa ba tare daya shirya amsar da zai bawa mai turo sak'on ba, shi dai kawai yasan alhaki ne ya fara biyarshi tun yanzu, dama ance idan kayi da 'yar wani za ayi da taka kaima, a hakan kuma yana ganin ko da ace Raihan bata tab'a sanin d'a namiji ba to angama dashi tunda har akaga tsiraicinta, kai shi sam bai ma yarda da babu abinda ya faru ba, tayaya namiji zai samu hotonta haka babu kaya a jiki inhar ba wani abu ne ya shiga tsakaninsu ba? Yana tsaka da wannan tunanin wani sak'on ya sake shigowa cewa _"Tunda baka da lokaci na zanyi abinda ya dace, da fari zan fara tura hotan a wayar mahaifiyarta, daga nan kuma zan sake shi duniya ta gani, ni ba kud'i nake nema a wurinka ba, ka aurar da 'yarka kawai ga wanda ka zab'a mata."_ Sai lokacin ya kira lambar Saleem na d'auka ya canza murya Abbas kuma yace "Bansan ko waye kai ba, amma dai nasan baka nufi na da alkairi, dan Allah karka saki hotunan nan domin kar mutumcin 'yata ya zube, nasan gabarka ba zata wuce dani ba dan haka ka d'auki fansarka a kaina, dan Allah karta shafi iyalina." Cike da izza yace "Ka fad'i gaskiya, amma ka sani ba zan huce ba har sai naga ka tara taron jama'a zasu shaida d'aurin auren 'yarka." A tak'aice yace "Zanyi, zan d'aura mata aure da safiyar gobe da Abdul, ban buk'atar had'uwa da kai, amma dan Allah ka goge hotunan nan daga wayarka, ba mutumcin 'yata bace harda ni kaina." Cike da dariyar iskanci ya amsa da "Saina gani idan kayi abinda nace." Makullin mota ya zara tare da takardar da Ma'arufa ta bashi yayi gaba ya bar gidan, a hanya tunani kawai yake wanene kuma wannan? Shin tarbiyar daya bawa Raihan kenan? Meyasa haka ta fara faruwa dashi? Wayarshi ya d'auka ya duba takardar nan ya turawa Ma'arufa wannan kud'in, bayan kud'in sunje yana ganin tana kiranshi amma ya k'i dagawa harya isa gidan, falon Sameera ya zarce ya sameta zaune ta gama waya da Bashir tana tambayarshi ko yasan abinda ke faruwa, amma yace mata bai sani ba tun jiya ma da rana rabon da su had'u, tana ganinshi ta mik'e da sauri tana fad'in "Abban Ameer sannu da zuwa, lafiya ka fita daga gida cikin sauri haka?" Saida ya kalli falon da kyau kafin ya kalleta yace "Idan Raihan ta zo kice ta same ni a falo na." K'ofar da zata sada shi da falonshi ya nufa ita kuma tace "Raihan kuma? Amma ai bata nan, ko ka manta ne?" K'ala baice mata ba harya shige, ita kam mamaki da damuwa ne suka hanata zama sai kai da kawowa, haka yara suka dawo daga islamiyya suka sameta, kiran Harira tayi ta had'a ta dasu ita kuma ta ci gaba da tunani, tana haka taji sallamar Raihan, tana juyowa ta ganta da jaka ta kinkimo cikin doguwar riga sai d'an siririn d'an kwalin data d'ora, da sauri ta k'araso ta rumgumeta tace "Ammie na, ya kike?" D'agota tayi daga jikinta fuskarta cike da damuwa tace "Mamana lafiya? Meyake faruwa ne? Ya kika dawo haka kwatsam? Meyasa Dadynki ke nemanki?" Cikin sanyi tace "Ammie i don't know, nima kawai Dady ya kirani a waya yace nayi gaggawa na zo, i hope komai lafiya?" Girgiza kai tayi tace "Ba nace ba Mamana, amma kije yana son ganinki a falon shi." Ba tare da tunani ko damuwar komai ba ta aje jakarta ta nufi k'ofar tana fad'in "Ok Ammie." Da sallama ta shiga falon, ganinshi zaune ya d'ora gwiwar hannunshi kan k'afafun shi kanshi k'asa ya had'e hannaye, sai kuma k'afafun shi da yake d'an bunbugasu, sallama uku tayi amma bai iya amsa mata ko d'aya ba, tsoro ne ya fara ziyartar ta amma a haka ta k'arasa kusa dashi ta zauna k'asa cikin taushin murya da sanyi tace "Dady?" D'ago kai yayi ya sauke kanta, gabanta ne yayi muguwar fad'uwa saboda ganin idonshi jawur kamar yayi kuka, mik'ewa yayi ya shiga bed ya dawo hannunshi rik'e da wata sharb'eb'iyar waya data sanya gudun gabanta tsananta, yana zuwa zaune ya sake yi ya kalleta ya d'auki wayar shi ya mik'o mata cikin rawar murya yace "Raihan waya d'aukeki hotonan?" Hannu tasa ta karb'a danta gani, da sauri ta dafe k'irji ta d'aga kai ta kalleshi sai taji wata kunyarshi ta rufe ta, sake kallon hoton tayi ta k'ura musu ido, ita ce ke wanka kuma ba'a ban d'akin gidan nan ba na basraba, to kenan waya d'auke ta? Waya bibiyeta haka? Tana cikin kallon taji tsawa daga Abbas tare da kashe ta da mari yana fad'in "Nace waya d'auke ki wannan hoton? Gaban wani d'an iskan kika tub'e?" Sakin wayar tayi ta dafe kunci hawaye wani na bin wani ta kalleshi a firgice, d'an siririn hannunta ya fizgo ta matso daf dashi cikin k'arajinmurya yace "Ba dake nake magana ba Raihan? Ke yanzu har ni zaki zubarwa da mutumci? Ina ganinki luf-luf yanzu nan ke har kinsan namiji? Raihan meyasa baki fad'a mana kina son aure ba? Amma shine zaki fita waje kina iskanci har ana d'aukar ki ana turo min da hotunan." Tsaye ya mik'e ya fara zabga mata bulalar nan baji ba k'akk'autawa, Raihan da zafi ya ratsata ta ko ina kuka take tana fad'in "Wallahi Dady ban san waya d'auki hoton nan, ka yarda dani ban tab'a iskanci ba a rayuwata, dan Allah Dady kayi hak'uri karka kashe ni." Sameera da taji kukan Raihan da gudu ta shigo falon, ta taho a sukwane zata tunkarosu ya d'ago ya d'aga mata hannu da cewa "Wallahi kika k'araso nan dake zan had'a." Tsayawa tayi tana kallo ya sake cin gaba da dukanta yana fad'in saita fad'a mishi ubanwa ya koya mata iskanci, da gudu Sameera ta sake fita sai part d'in su Ammie, ta sameta tana shirin kabbara sallah azahar, ai tana fad'a mata suka rankayo tare suka shigo, da k'yar Ammie ta dakatar dashi kafin ya tsaya cikin b'acin rai ya kallesu yace "Ko ku shirya ko karku shirya gobe zan aurar da ita kafin ta ja min abin kunya." Bed d'in shi ya shiga Sameera tayi kan Raihan dake kwance tana kuka, kamata tayi cike da tausayi tana kallon jikinta da duk ya canza ya fita hayyacinshi, tashinta tayi suka tafi d'akin ta ta kwantar da ita, zage mata zuf d'in rigarta tayi ta cire mata ya rage sai bras d'in ta da pant kawai, kallonta Sameera tayi da kyau tace "Raihan ki fad'a min gaskiya, shin kin watsar da tarbiyyar da muka baki ne?" Zaune tayi ta janyo blanket d'in kan gadon ta rufe jikinta tana kuka tace "Wallahi ban zubar ba, Ammie bansan ya akayi hoton tsiraici na ya fito ba, Ammie ki yarda dani dan Allah." Sunkuyar da kai tayi tace "Ba zan iya yarda dake ba Raihan, domin kuwa yaran yanzu ka haifesu ne baka haifi halinsu ba." Ammie dake tsaye ne cike da jimami tace "Ki had'a mata ruwa tayi wanka." Mik'ewa Sameera tayi inda Ammie ta kalli Raihan da duk jikinta ya sauya tace "Kinsan da gobe yace zai d'aura aurenki da Abdul?" Da sauri ta kalleta kamar zatayi magana sai kuma tasa kuka tace "Ammie ba damuwa na amince, ni kuma zan tabbatarwa da iyayena a budurwa naje gidan mijina." ♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Tun daren jiya Ma'aruf daya fad'awa Meena aikinsu ya kammala ta dinga saka mishi wani tunani tana nuna mishi dukiyar nan fa kamata yayi ace tashi ce shi kad'ai, farko baisa abun akai ba dan ba zai iya cutar da yar uwarsa akan dukiya ba, amma da dare suna zaune d'aki shi da Ma'arufa ya kalleta yace "... 👏👏👏 22/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💞 _Kyautarku ce_💕 *Momyn Dady* *Lubabatu Shehu Shayi* *Umman Modee* *Sis Chappa* *Zeinab* *Hafsat Yahaya Ali* *Choukra* *A~A~S~* *Maman Abulkhairi* *Voisine Ruky* *Maman Tasleem* *Aisha Gimba* *Rafi'a* *Wahabijubaina* *Hafsat Uba* *Soumayya mahaman kaka* *Ummu Khairat* *Maman Chapa'atu* *Fasma* 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _20_ "Gaskiya nayi farin ciki sosai da kuka amsa kira na, dama kuma nace su turo iyayensu ne domin a samu fahimtar juna sosai, yanzu Alhamdulillah zamu iya tsayar da magana." Lieutenant ne yace "Hakane Alhaji, kuma dama ai mu ya kamata mu fara zuwa Allah bai nufa ba sai yaran, amma yanzu mun zo muji da kanmu daga bakinku." Wani hukuncin ubanjigi sosai Labaran ke kallon tsohon saboda zamansu iri d'aya ne irin zaman rak'uman nan, kawai kamar had'in baki sai suka sa hannu suka d'an tura hularsu baya suka shafi goshi, tsam colonel yayi da ido ya kallesu ganin sunyi abun a tare kamar sun tsarashi dama, shi kanshi Labaran satar kallonshi yayi amma malam Rabi'u bai kula da hakan ba, nan suka ci gaba da tattaunawa suka tsayar da magana inda lieutenant ne yace "Idan har zaku lamunce mana zamu so ayi bikin nan da wata d'aya, da yake akwai sauran yan uwanshi da suma duk za'a aurar dasu nan da wata d'ayan, shiyasa muke so ayi lokaci d'aya a gama." Malam Rabi'u ne ya kalli yan uwan mahaifin Maryama da kuma yayan mahaifiyarta kafin yasa hannu ya maido da hularshi inda take wanda yayi daidai da Labaran ma ya dawo da tashi hular, cikin fara'a yace "Wannan ai ba wani abu bane, dama dalilin da yasa muka nemi ku zo kenan, dan haka ba wani abu kawai." Farin ciki sukayi inda lieutenant yace "To dama a shirye muka zo, dan haka." Colonel ya kalla da Labaran suka d'anyi k'usk'us kafin su kalli Junaid dake can gefensu, mik'ewa yayi ya fita jim kad'an saiga yara matasa suna shigo da akwatina masu kyau guda bakwai da kuma goro, nan suka tsayar da ranar daidai da sauran bikin tare da bayar da duk abinda ya dace, girkin da akayi dominsu aka fito musu da shi, har zasu fara ci sunawa juna bismillah muryar Labaran da malam a tare suka ce "A'a Alhamdulillah, ai ni bana cin naman tsintsaye." "A'a Alhamdulillah, ai ni bana cin naman tsintsaye." Wannan lokacin kallon juna sukayi a tare, murmushin da sukayi ne ya bayyanar da wani tabo dake fitowa a duka fuskokinsu a duk sanda sukayi dariya a gefen kumatunsu na dama, gaban Labaran ne yaji ya sake fad'uwa, amma banda malam da shi ko a jikinshi ma, haka dai suka gama cikin mutumta juna da girmamawa suka sake dawowa. *Tun* daren jiya Alhaji ya d'aure wa Hajia yace fa babu fashi auren lieutenant, a k'arshe ma cewa yayi ta mishi lissafin abinda za'a buk'ata ya bayar, kamar wasa kuwa da safe haka ya sake sakata gaba saida tace kawai ya bada duk abinda yaga dama, aifa nan ya bata mamaki ta hanyar bata babbar enveloppe da kud'i har million uku ciki yace tayi idan ma basu isa ba tayi magana ya k'ara mata, sai ga Hajajju na kira a waya harda fita ita da drebanta wajen siyo kayan lefe da saurensu, amma ji take kamar ta mutu dan sam Zeituna bata mata ba, tana ganin bata dace da ajin d'an ta ba duk da yanzu d'an nata ya zama tsoho. 😛 Da yamma Alhaji ya had'a kan yan uwa da abokan arzik'i suka kai akwati guda goma sha shida wanda kowace saida aka mata k'at da kaya a ciki gidansu Zeituna da goro salka biyu da kuma 1 million kud'in d'inkin kaya, kad'an ya rage Zeituna ta mutu tsabar bugawar da zuciyarta tayi, ita fa har yau a mafarki take ji da kuma ganin abun, ba zata tab'a yarda wai lieutenant ne zata aura ba, nan fa unguwa ta d'auki tsegumi k'asa k'asa anayi, wasu na fad'in ya siyar da ita saboda kud'i, wasu na fad'in kawai akwai surkullen da akayi har babban mutum kamar wannan ya kalli Zeituna yace yana sonta, to haka dai akayi aka gama Hajia ita ma kamar ta mutu. *Ammar* na gama cin abinci ya kalli aunty yace "Aunty zan d'an fita, watak'ila ma na wuce ta wajen mutumin (mijinta) dan nasan akwai hira a bakinshi." Dariya tayi tace "Ai kam kamar ka sani, kasan shi baka raba shi da zance, amma kafin nan muyi hira mana." A tsanake ya kalleta ya sauke ajiyar zuciya, d'orawa tayi da "Ammar meke faruwa a gida? Tun shigowarka na hango damuwa tare da kai, sannan ga hannunka da bandeji, bugu da k'ari baka tab'a zuwan safe irin haka ba." Wata ajiyar zuciya ya sake saukewa amma baice komai ba, hakan yasa tayi murmushi tace "Hajia ce ko? Ammar ou dinga hak'uri da ita wata rana sai labari, ka duba ni ka gani mana, yanzu haka fa su Hamna sunfi shekara d'aya rabonsu da nan, kuma sun fad'a min suna son zuwa Hajia dai ce bata amince musu ba, amma kaga nayi hak'uri duk da cewar bayan rabuwata da mahaifinsu dana auri *Shu'aib* bamu samu haihuwa ba har yanzu, amma hakan baya damu na tunda ina tare da wanda zuciyata ke so, kaga dai ba cikin birni nake ba, sannan ba cikin daula ba kamar gidanku, amma wallahi hakan yafi min komai, kaima da wannan nake shawartarka da akayi hak'uri, idan ka samu wacce kake so sai kaga komai ya wuce." Cike da gamsuwa da bayaninta ya kalleta yace "Aunty wannan karan ma ba Hajia bace Alhaji ne, wai aunty jiya Alhaji yake cewa wai ya nemawa Abba auren yarinyar nan yar aiki, Zubaina take ko uwar wa ma? Kuma wai za'a d'aura auren ranar juma'a ta gobe, kiji fa?" Ita kanta wani banbarak'wai taji abun, amma sanin halin yaron nata yasa tayi murmushi tace "To yarona meye na tashin hankali a ciki? Shi aure ai lokaci ne, nasan kuma kasan da haka, sanin kanka ne duk iyayen nan naku matansu d'aya d'aya ne, tunda har yanzu Alhaji ya yanke wannan hukuncin to ku rumgumi k'addara mana, watak'ila fa tsananin rabo ne, kuma inhar ya kasance rabo ne to ka sani wallahi ba kai ba ko Hajia ce tayi yunk'urin hanawa wannan rabon zai iya halakata, ko da kuwa zata gitta masa tsinuwarta ce, dan rabon 'ya'ya idan ya koka wallahi sai sun zo duniya ko duka mutanen duniya basa so, dan haka ni dai abinda zan shawarce ka dashi shine kuyi hak'uri dan Allah, kar ka d'agawa iyayenka hankali Ammar, kuyi fatan yarinyar ta zama alkairi ga mahaifinka kawai da kuma mahaifiyarka." Kallonta yayi a nutse yace "Shikenan Aunty, ni zan fita saina dawo." Mik'ewa yayi ya saka takalminshi ta kalleshi tace "Baka fad'a min cewa Hajia ta zab'a muku yan uwanku ba?" Murmushi yayi kawai ya shafa sumar kanshi ya fice, girgiza kai tayi dan tasan bai gamsu da abinda ta fad'a mishi ba, yana fita kuwa shawagi ya dinga yi ya jima bakin ruwa yana kallon gudanarsu, daga nan kuma ya zarce bakin kasuwa wajen mijin auntyn suka sha hira, a tak'aice tare suka wuni har yamma suka dawo gida, nan ma wani shafi hira suka bud'e kamar d'a da uba kafin daga bisani zuwa *05:56* ya d'auko hanya, saida yayi sallah ya wuce gida kai tsaye da tunanin wacce zai samu kuma yau. *Bayan* dawowarsu da yamma Labaran na d'akin mahaifiyarshi da abinci gabanshi amma tunani ne fal a ranshi, lura da hakan yasa Husseina kallonshi cike da kulawa tace "Ga damuwa ina gani a fuskarka, sai dai bansan dalilin da yasa kake son b'oye min ba?" Da d'an murmushi ya kalleta yace "Ba komai Hajiata, kawai dai gajiya ce sai kuma yau da gobe." Murmushi itama tayi kawai ta share maganar, d'ibar wata loma yayi zai kai baki sai kuma ya tsaya ya kalleta saboda tsikararsa da zuciyarshi tayi yace "Hajiata, zan iya tambayarki wani abu?" Kallonshi tayi tace "Zaka iya mana, ina jinka." Kallonta yayi yace "Hajia kiyi alk'awarin ranki ba zai b'ace ba da tambayar da zan miki?" Annurin fuskarta ne ya b'ace ta kalleshi da kyau tace "Ka fad'a ina jinka." Cike da fargaba ya d'anyi k'asa da kanshi yace "Hajia dama...dama in..ina son...sanin..cika...kken bayani...ne akan..." Shiru yayi ya kalleta hakan yasa ta kalleshi tace "Akan me kake son sani?" Sauke kanshi yayi yace "A...kan mahaifi na." Saida ya sauke wata ajiyar zuciya mai nauyi saboda abune da shi dai rabon daya fad'a tun yana shekara ashirin da biyar a duniya, k'ura mishi ido tayi tana kallo wanda hakan ya haifar da zubar hawayenta, hijabinta ta saka tana share hawaye, a tsorace ya matsa kuma da ita yasa hannu yana share mata hawayen yana fad'in "Dan Allah Hajiata kiyi hak'uri ki gafarce ni, Hajiata ki daina zubar da hawayenki dan Allah indai akan abinda na fad'a ne, na hak'uri da son sanin abinda nake son sani." Cikin kuka da son bayyanar da abinda ke ranta tace "Alhaji mahaifinka ya cuceni, ya cutar da rayuwata, ya lalata min k'uruciya ta, sanadiyar abinda ya aikata min har yanzu nake zaune a matsayin bazawara, mahaifina har ya mutu yana hushi dani saboda abinda ya faru dani, Alhaji meyasa zaka min maganar shi? Wannan tsinann..." Da sauri ya rufe mata baki saboda jin hakan ba zai mishi dad'i ba, duk da ta hanyar da bata dace aka same shi ba kuma bai ma san waye mahaifin nashi ba, amma dai ba zai so jin tsinuwarta akan shi ba, hak'uri ya dinga bata yace ba zai sake maganar ba ta hak'ura kawai, saida tayi shiru ta kalleshi tace "To ka ci abincin naka." Da sauri ya koma kan kujerar yace "To Hajiata zan ci, kiyi hak'uri dan Allah." Nan ya fara aika abincin ba dan yana masa dad'i ba sai dan faranta mata rai kawai. Ana idar da sallah magrib Hamna ta shirya zuwa kan amarya ba tare da kowa yasan fitarta ba a gidan, Husseina ce a falo zaune ta k'walla mata kira saboda sunyi magana da Alhaji akan hidimar bikin lieutenant, yanzu haka ta kirata ne dan taje ta siyo mata pliwa dasu sukari da sauran kayan had'in biscuit da cincin na tarban bak'i, Amna dake kwance kan gado da doguwar riga bak'a da kallabinta, rigar ta mata kyau sosai ta fito mata da gwagwab'an mazaunanta da k'irarta, tashi tayi ta fito tana amsawa a matsayin Hamna (baki daddara ba kenan)?, tana zuwa ta zauna kusa da ita tace "Hajia gani." Kallonta Husseina tayi ita dai bata ga wani banbanci ba, domin kuwa akwai kwalliya a fuskarta wacce ta b'oye duhun da take dashi, sai dai bata ga dogon gashi kwance a baya ba, k'aramar jakar hannunta ta d'auka ta fito da kud'i ta mik'o mata tace "Hamna wajen *Ilu* zakije ki siyo mana wannan kayan." Ta fad'a da mik'a mata takardar da tasa aka rubuta mata kayan dan karta manta ita ma. Amsa tayi tace "To Hajia." Mik'ewa tayi ta shiga d'akin su ta d'auko makullin moto ta fito, har ta wuce Husseina tace "Hamna." Cak ta tsaya da tunanin ko ta ganeta, a hankali ta juyo ta kalleta ita kuma tace "Yau wace rana Hamna na aike ki baki ce a kawo kud'in mai ba." Wurga yan matsakaitan idonta tayi ta sauke b'oyayyar ajiyar zuciya tace "Hajia ai akwai mai." Girgiza kai Husseina tayi tace "Dama can ai iskanci ne kesa kike cewa babu mai." Yanda tasan idan Hamna ce za tayi haka kuwa tayi sumbatar hannunta tayi ta jefa ma Husseina tace "Saina dawo sai ki biya kud'in aiki." Da murmushi kawai ta bita har ta fice, motonta ta hau ta tsaya bakin k'ofa tayi oda wanda yasa mai gadi bud'e mata k'ofa, ta murd'a zata fita kenan motar Ammar ta kutso ciki shima, yanda hasken fitilun motar ya d'auke mata ido yasa tasa bayan hannunta ta rufe ido, ganin haka yasa ya k'i kashe hasken sai k'urawa bakinta ido da yayi wanda shi kad'ai ya fito fili, a hankali ya lumshe ido saboda wani tunani da yayi yanzun nan, ina ma ace matarshi ce shi kam da ya samu nutsuwa a tare da ita a halin da yake ciki na rashin dad'in nan, kashe hasken yayi ya lek'o da kanshi ta gilashi yace "Sai na zo na d'auke ki ne dake da moton?" Da sauri ta sauke hannunta ta kalleshi tana girgiza kai, gabanta ne ya fara fad'uwa inda jikinta na rawa ta kau ce mishi a hanya, da kallo ya bita a hankali ya furta " *Amna* kenan." (Wato ya gane wacece) Jira take ya wuce ko ta samu ta fita amma taga baida niyyar haka, muryarshi taji yace "Ina zaki?" Da tsoro fal a fuskarta da kuma muryarta tace "Hajiarsu Jibril ce ta aike ni shagon Ilu?" Wani kallon babu wasa ya mata yace "Ki aje moton ki zo muje na kaiki." Bud'e baki tayi cike da bayyanar tashin hankalin zatayi magana sai kuma ta tuna waye gabanta, ruf ta rufe bakinta ta d'an jinjina kai alamar to a zuciya kuma tana fad'in "Kin mutu Amna." Komawa tayi ta aje moton ta dawo, yana kallon kowace gab'a ta jikinta harta bud'a gidan gaba zata shiga, zata zauna taga wani kallo da yake mata kamar na bansan iskanci, hakan yasa ta rufe k'ofar ta kama murfin baya zata shiga, a tsawace yace "Dan ubanki waye dreban naki? Ni ko uban wa?" Da sauri ta rufe jiki harya fara rawa ta bud'e gaba ta zauna, yanda ya kafeta da ido yasa yake iya fahimtar yanda take sauke numfashinta kamar wacce tayi gudu, jin bai tayar da motar ba yasa ta d'an d'ago kai ta kalleshi. Tana kallonshi ya fizgo d'an kwalinta ya jawo kanta ya matse a tsakiyar hammatarshi yasa kallabin ya fara darzar mata fuska yana fad'in "Bak'ar munafuka aiken Hajiar ne zakije sai kinyi kwalliya? Ko yau ma a matsayin kankanar kika fito daga gidan?" Saida ya gama ya tureta ya jefa mata d'an kwalin, da k'yar ta bud'e idonta saboda tumurmusar da fuskarta tasha, d'aukar kallabin tayi ta d'ora akai a lokacin sun fara tafiya, babu mai magana su dai a haka suka isa shagon Ilu, fitowa tayi ta tunkari shiga shagon, Ammar dake kallonta ganin yanda rigar ta fito mata da surarta ga kuma wani namiji a cikin shagon shima yana siyayya hakanne yasa shi jin wani takaici, tsaki yayi ya daki sitiyarin motar yace "Uban wace ta fito a haka ma? Wato kankana zata koya miki ko?" K'wafa yayi yana ci gaba da kallon yanda take murmushi suna gaisawa da wannan mutumin, wanda rabon ayi ne kawai yasa Amna gaishe shi ya amsa, ya gama siyayyarshi ya kalleta yace "Hajia sai anjima ko? Gashi zamu rabu bansan ko sunanki ba?" Murmushi tayi tace "Allah sarki yaya na, suna na Amna." Cike da zolaya yace "Amna zanyi mata ta biyu dake idan kin amince? Ko zan samu lambar wayarki?" Jim ta d'anyi tana kallonshi hakan yasa ya mik'o mata wayarshi yace "Da gaske fa nake, ki taimaka ki saka min sai muyi magana a waya ko? Dan bai kamata muyi magana akan titi ba." Ammar da tunda yaga hirar ta k'i k'arewa gashi dama tun jiya yake neman abokin masifa sai yaji kawai yarinyar ma ta raina shi, a fusace ya fito ya nufi shagon, kafin ta karb'i wayar Ammar yayi wuf da ita sai kuwa yayi cillin tsiya da ita akan titi, mutumin bai gama fahimtar meya faru ko zai faru ba sai kuwa yaji Ammar yayi sama da shi ya dasa a k'asa, kafin dai ya ankara da abinda ke faruwa Ammar ya fara kai mishi naushi a fuska yana fad'in " Kai kwarton ina ne? Daga ganin yarinya kawai sai yi mata magana, kasan wacece ita?" Ledar dake rik'e a hannun mutumin wanda yanzun akayi fatali da ita Ammar ya jawo, hannu yasa ciki ya rarumo wata leda kamar balam-balam ya buga mishi a fuska, sai kuwa man gyad'ar dake cikin ledar ya tarwatse a jikinsu dukansu, Ilu dake ta k'ok'arin d'aga Ammar daga jikin mutumin da shi yake k'ok'arin ya tashi amma Ammar ya hanashi damar hakan, mutanen dake kusan nan ne suka sukwano da gudu suka zo rabo, da k'yar suka tayar dashi daga jikin mutumin shi ma ya tashi, fad'i yake "Matar tawa zaka wa iskanci? Qur'ani saina kashe ka." Jin yana fad'in matarshi ce yasa mutanen ganin kamar waccen mutumin ne baya da gaskiya, dan haka suka jawo Ammar da k'yar suka turashi motar shi, Amna dake tsaye cikin shago har ta fara shashek'ar kuka wani ya kalleta yace "Dan Allah madame ki wuce ku tafi, ki samu ki kwantar masa da hankali, kuma ko da kunje gida kada ki biye masa, dan halin da yake ciki zai iya illataki." A firgice ta sake kallon mutumin tana maimaita kalmar " *Illataki*." Tasan babu abinda zai hana ya illatatan kuwa, dan haka ta girgiza kai tace "A'a, ya tafi kawai zan zo a bayanshi." Daga cikin mota Ammar yake iya fahimtar me Amna ke nufi, sake dantse leb'en shi na k'asa yayi bala'i kawai yake nema da mai yi, ganin bata da niyyar fitowa yasa shi fitowa daga cikin motar da k'arfin bala'i ya tunkari shagon, wannan mutumin da mutane suka zagayeshi har da Ilu mai shago saida gabanshi ya fad'i dan ya d'auka wurinshi ya koma, kai tsaye cikin shagon ya shiga, Amna na ganin haka ta durk'ushe ta had'e hannayenta tana fad'in "Ka dubi girman Allah y..ahhhhhh." Ta saki k'ara saboda jawo hannunta da yayi da k'arfi, saida ya bud'e motar ya wurgata ciki ya zagayo ya shiga, da wani irin bala'in gudu ya fizga wanda yasa hankalin mutane dayawa komawa kan motar, wasu tuni suka fara jin tausayin yarinyar dansun san wannan ta shiga uku. Saida sukayi nisa inda babu mutane ya taka birki ya kalleta a matuk'ar zafafe ya daki k'irjin shi yace " Amna ni zaki rainawa wayo? Ni zaki wulak'anta a idon jama'a? A gaban ido na ki tsaya hira da wani har kina neman bashi lambarki, bayan kuma kinsan ke d'in *tawa*, tawa ce mallaki na, ko gani kikeyi waccen banzan zai fini iya hawa ruwa cikinki ne? Gani kike zai fini iya sukuwa a kanki kenan?" Amna banda girgiza kai babu abinda takeyi, a fusace ya kwad'a mata marin da yasa jinta d'aukewa, ta dafe kunci kenan taji ya shak'o wuyanta da hannu biyu, cikin azaba ta zaro ido ta kama hannayen nashi da nata hannayen taa neman ya saketa ta numfasa, cikin k'aramin lokaci ta fara fafutukar neman numfashi dan ba k'aramar shak'a ya mata ba, shi kuma cikin hargagi ya kawo bakinshi daf da hancinta yace "Saurare ni da kyau Amna, ke da gangar jikin ki nawa ne, duk da akwai inda zuciyata tafi karkata, amma ki sani tunda kakarki tace ta bani ke wallahi kin zama tawan, saina moreki ko da baki son haka." Wurgata yayi saida kanta ya bugu ga gilashin motar, k'asa tayi da kanta tana sauke numfashin wahala, jan motar yayi suka isa gida, yana paka mota ta fito da sauri ta nufi falon Hajia, ganin yanda kunkuminta ke juyawa ya k'ara tunzurashi, kenan shima waccen mutumin abinda ya gani kenan? Ai da sauri ya fito yana fad'in "Ke ke! Zo nan." Tsayawa tayi ta kasa motsawa tana kallonshi wasu hawayen na zubowa, yana kawowa daf da ita ya kamo rigarta yace "Uban wa ma yace ki fito haka? Iyee! Wa yace ki fito haka kina tallar kanki?" Shiru tayi sai sharar hawaye da take, haushi ne yasa shi ciro takalmanshi ya gaura mata a fuska, wata razananniyar k'ara ta saki ta dafe kunci, sake jibga mata shi yayi a baya hakan yasa ta zabura ta zube kwance a wurin, k'afa yasa ya fara harbinta yana fad'in "Wannan rigar data dace ki fita da ita ce? Ke bari kiji daga yau ba zaki sake fita daga gidan nan ba, kinji ni ko." Jin kururuwar Amna yasa mutanen gidan fitowa suka kawo mata d'auki, ganin abinda ke faruwa yasa Ummy tahowa da gudu ta durk'usa ta rumgumo Amna, babu namiji ko d'aya a gidan sai yaran hakan yasa Ummy kallonshi cikin b'acin rai tace "... *Addu'arku yan uwa.* 👏 22/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _12_ Ma'aruf ne yace "Wai ke yaushe ne zaki fito da kud'in nan a raba kowa ya kama gabansa?" Ba tare data kalleshi ba tace " Kana gaggawa ne da son samun naka kason?" A d'an hassale yace "Ban gane? To idan ba'a raba ba uban kud'in zasuyi a account d'in? Kinga ki fito dasu kawai kowa ya d'auki nashi ya san inda dare ya masa." Aje wayar tayi ta zaburo tace "To idan fa na k'i? Ai dai kasan kud'in a account d'ina aka saka ko? Kuma sai ni ce ke da damar cirewa? Dan haka ka bini a hankali har lokacin da naga dama sannan na fito dasu mu raba." Shima tasowa yayi yace "Wallahi baki isa ba, ni zaki d'auka d'an iska, wato kinga kud'i kenan shine zaki nemi ki raina min hankali? To baki isa ba wallahi, kinsan ko k'arfi ne zansa na karb'a." Da k'arfi tace "K'arfi? K'arfi fa kace? Wai kai ka ma san wahalar da nasha kafin a samu kud'in, kana nan zaune nasa kaina a had'ari wanda da sun gano ni me kake tunanin zai faru da ni? Haka na kwashe kwanaki a gidan ina tunanin abunyi har na cimma nasara, kasan ta yanda akayi na shawo kansa ne? Da k'yar ya kwanta dani shima bayan na ci maruka daga gareshi, haka ya shigeni babu imani ya sussuke ni, duk kai kana nan zaune kuma shine yanzu zaka wani bud'e min ido, to bari kaji da kyau tunda abun na ka ya zama iskanci, wallahi kud'in nan ko sisin kwabo ba zan baka a ciki ba, sai dai na maka alk'awarin zan karb'o maka ko million biyar ne ko goma a wurinshi, dan na fahimci baisan zafin neman kud'i ba." Sai lokacin maganganun Meena suka fara dawo masa da tace ko ita Ma'arufa ta samu yanda zatayi ta cinye kud'in ita kad'ai to zatayi ne, dan haka shi ya mik'e ya karb'i kud'in inba haka ba zai zama d'an kallo, wani iska ya furzar daga bakinshi ya jinjina kai yace "Shikenan, ki samo min million goman, ke saiki rik'e waccen d'in." A wulak'ance ta kalleshi tace "Ai na d'auka zakayi gardama ne?" Murmushin mugunta yayi yace "Gardama tame kuma? Abinda ba kai ka tara ba." Mik'ewa yayi zai fita yace "Yaushe kenan zan saka rai?" A yamutse tace "Zuwa gobe zan masa magana, yanzun ma dan dare yayi ne." Baice komai ba ya fita ya barta, daga nan kuma hotel d'in da Meena take ya zarce, tsaf ya fad'a mata komai, tab'e baki tayi tace "Ai dama na fad'a maka, yanzu kawai lambar account d'in nata zaka samo mana, ni inada mutanen arzik'i sosai a garin nan, zamu san yanda za'ayi a maka transfert d'in kud'in zuwa naka account d'in." Kallonta yayi yace "Amma yaya zamuyi haka alhalin tana raye?" Zaune tayi kan cinyarshi ta sagala hannunta ta bayan wuyanshi tace "Kalamanka suna so su nuna kamar ka d'au saiti? Ni kuma in hakane ina da maganin matsalarka." Juyawa tayi bayanta ta d'auko jakarta ta bud'a ta d'auko wani k'wayar magani mai kamar ampicillin ta bashi tace "Kawai ya gyauraya a abun shan ta." Karb'a yayi ba tare da tunanin komai ba kafin ya had'e bakinshi da na ta, suna lulawa nima na lulo nayi waje . Abbas da kanshi ya samu magabatan Abdul ya sanar dasu za'a d'aura auren gobe bisa wani dalili mai k'arfi, su kuma cikin farin ciki suka amsa mishi da ba komai ai Abdul d'an shi ne, shi kanshi Abdul d'in farin ciki yayi saboda zai mallaki abar son shi, yayin da zazzab'i kuma ya rufe Raihan baiwar Allah, har likita ya zo ya dubata ya bata magani, tana kwance d'akin Sameera tana bacci, ita kuma Sameera shiryawa tayi cikin kayan baccinta taje bed d'in shi, tana shirin yin kwance yace "Idan ba damuwa ki koma d'akin ki mana?" Da mamaki ta kalleshi tace "D'aki na kuma? Kana gari me zaisa mu raba shinfid'a?" A k'ufule yace "Haka nake buk'ata, ina buk'atar kad'aici." Matsawa tayi kan kujerar da yake zaune ta sunkuya ta kama hannunshi cikin magiya tace "Sir, dan Allah ka fad'a min meke damunka mana? Ni fa matarka ce, Sameera, ko ka manta ne? Idan ni nayi maka laifi dan Allah ka fad'a min saina baka hak'uri, idan kuma kana hushi dani ne kan maganar haihuwar da kake so, na amince ka bar hushin dani, muje sai ka min cikin mana na shirya d'auka, amma bana son hushinka wallahi." Rintse ido yayi yana jin kamar ya k'ona kanshi yace "Bana jin zan sake haihuwa da ke." Dam! Taji gabanta ya fad'i yayin da ta kafeshi da ido da alamar tambaya, da tsantsar mamaki tace "Baka son sake haihuwa da ni? Akan me? Me nayi maka da zafi haka? Abban mama na yaran da muka haifa fa? Yanzu har girman zunubin dana aikata ya kai ka fad'a min wai ba zaka sake haihuwa da ni ba?" Cike da k'osawa yace "Dan Allah ki fitar min daga d'aki." Had'e kukanta tayi tace "To zamu iya yin magana akan matsalar 'yarmu?" A tak'aice yace "Ba zamu iya ba." Kallon fuskarshi tayi tace " 'Yar mu ce fa? Girman laifin data aikata yasa har ka daki yarinyar da ko tsawa mai k'arfi baka tab'a mata ba, sannan ka ce zaka aurar da ita gobe, kana ganin hakan ya dace?" A gajiye ya kalleta yace"Ya dace Meerah, please ki bar ni nasha iska mana." Mik'ewa tayi jiki a sanyaye ta kalleshi tace "Sorry." Juyawa tayi inda ya rintse ido matuk'ar tausayinta ne yaji ya mamaye shi, saida yaji ta rufe k'ofar d'akin ya juya ya kalli k'ofar wasu hawaye suka taho mishi yace "Sameera ba zan yarda na sake had'a jikina da na ki ba, nasan zan cutar dake a hakan, amma k'azamin jikina ba zai sake tab'a tsarkaken jikinki ba, Sam ki yafe min, ba zan iya fad'a miki komai ba, domin kuwa nasan a ranar ko baki kashe ni ba zaki cutar da kanki, ba zan bari ki kashe ni ba dan bana son ki shiga wuta dalilin banza iri na, ba kuma zan yarda ki cutar da kanki ba." Tana shiga d'aki ta samu wayarta na ta kururuwa sarki Imran ne, d'auka tayi ko gaisawa basuyi ba ya fad'a mata abinda ke faruwa a masarauta. *Basraba* Bayan tafiyar Sameera sai kuwa waziri ya taso uwar d'aki gaba akan dole fa ayi auren nan da gaggawa, ya gama tsorata da recoding d'in da yayi tare da mata barazanar zai ce ita ta saka shi ya kashe takawa, nan fa jikinta ya d'auki rawa ta fara neman mafita, amma a k'arshe dai mafitar bata wuce tayi abinda yake so ba, nan ita ma ta tasa Imran gaba sai anyi aure nan kawai nan da kwana biyu, wanda yanzu ya kasance gobe za'a d'aura, Imran ya kira Abban Sameera amma yana hushi akan abinda ya faru yasa ya k'i d'aga kiranshi , dan haka ya kira Sameera dan ta fad'awa Abba akan ya zo ya dakatar da auren nan, shi bai ce ba zaiyi ba amma ba zaiyi aure ba kwana shida da rasuwar mahaifinshi, amma Sameera sai tace mishi kawai ya amince a d'aura dan a zauna lafiya, nan sukayi sallama kowa yaji da abinda ke damunshi. *WASHE GARI* Lafiya lau aka d'aura auren sarki Imran Musayyib Ali da matarshi ta farko *Safiyya Ahmad* da kuma mata ta biyu *Jawahir Ya'u* dukansu akan sadaki dubu hamsin hamsin, hankalin waziri ya kwanta kam dan yanzu ne burinshi zai cika, a wautar uwar d'aki ita ma tana ganin hankalinta ya kwanta tunda asirinta ya rufu yanzu, yayin da gimbiya Ameera tayi kuka sosai jin auren mijinta kamar a mafarki, tsawon lokaci ya d'auka yana rarrashinta da bata hak'uri da fad'a mata duk abinda ya faru, yayin da ake toya masa anan acan Abuja kuma ana toya wata masar ne. *Abuja* Kamar yanda Fadila ta samu labarin d'aurin auren Raihan a tsakiyar dare haka ita ma ta dokowa Abdul kira a dugun-dugun safiya, bayan ya d'auka ne ta fashe da kuka tana fad'a masa ita fa son shi take ya taimaka mata, cikin ruwan sanyi yake lallab'a ta yana bata hak'uri saboda akwai mutumci tsakaninsu, amma sai baud'ewa take tana fetsarewa, a k'arshe ma zuciya ce ta deb'eta tace "Yanzu kai ka d'auka zasu baka yarsu dan suna sonka ne? To ba gaskiya bane, soyayyar da suke nuna maka ta bogi ce yayin da a ransu babu hakan ko kad'an, sun d'auke ka kamar bawansu ne wanda suka siya da kud'i, Raihan ita ce rayuwarsu, hakan yasa suka tanadar mata kai dan rayuwar gidan aurenta ta mata dad'i kamar yanda suke so, a bayyane yake ai, inhar ka aureta ba zaka yarda ka muzguna mata ba ko ka mata ko da kallon banza, to wannan ne dalilinsu na son had'a ta da kai, amma a bad'ini suna maka kallon wanda ko mai aikin gidan yarsu baka kai." Murmushi yayi mata yace "Idonki ne suka rufe har kike fad'in haka? To muje ma a hakanne, Fadila na amince zan auri Raihan, ai dama hallacin da iyayenta suka min bai kamata ace na harari ko da k'eyar Raihan ba bare gabanta." Cikin fitar hayyaci tace "Shikenan ka aure ta mana, ita d'in ka d'auka sonka take? To kaji da kyau zan fad'a maka ko ba zaka yarda ba, basu yarda sun had'a wannan auren ba saida suka saka aka maka gwajin jini a b'oye ba tare da saninka ba kafin suka yarda ma da maganar aurenku, saboda basu so ka lak'awa yarinyarsu cutar da mahaifinka ya d'auko ya kuma gogawa mahaifiyarku, idan kuma baka yarda ba Abdul kaje ka tambayesu, inhar ba k'arya zasu fad'a maka ba to tabbas zasu fad'a maka gaskiyar zancen." Cikin mamaki ya dafe goshinshi yace "Ke! Wai me kike nufi ne?" Cikin b'acin rai tace "Ban sani ba, kaje ka tambaya kaji, kai ka mayar da mutanen kamar ababen bautarka, alhalin kuma baka uya fahimtar mai sonka na gaskiya, ni ce ke maka so na hak'ik'a amma Raihan ko a tunaninka bata saka ka, ko da yake ai hausawa sunce *sanin masoyi sai Allah*." Tana fad'a ta kashe wayar ta cillar ta fashe da kuka, shi kuma zaune yayi bakin gado ya dafe kai ya shiga tunani, shaid'an nata d'awainiya da zuciyarshi sai kuma ga kiran Saleem (masu tambayar waye Saleem da Abbakar, Abbakar shine mijin daya auri Zeenat yar Tahir kawun Abbas), yana d'auka shima ya gama rikita mishi lissafi da nuna mishi Raihan budurwarshi ce ai, suna rayuwar soyayya kuma suna son juna, jiya kuma an kira mahaifinta ne an fad'a mishi an gansu tare a hotel a basraba, dan haka ya umarceta ta dawo, bayan ya nad'a mata na jaki kuma yayi gaggawar d'aukar matakin aurar da ita gare shi shi dake sakarai, nan yace idan bai yarda ba ya duba WhatsApp d'in shi zai gani, ganin wannan hotunan suka saka Abdul fashewa da kuka yana dana sanin yarda da yayi da iyayen Raihan, gashi tun jiya dama da kawunshi ya fad'a mishi halin da ake ciki ya dawo gida nan ya kwana, shiryawa yayi cikin shiga ta ango ya tafi da niyyar nuna musu shima ba kanwar lasa bane. Misalin *07:30* a masallacin k'ofar gidan aka taru dan d'aurin auren, bai wani samu mutane ba dan ba'a shirya ma hakan ba, dan wani abokin kasuwancin Abbas dake mutumin Niger ne ma masifa ya dinga yi wai ya zai aurar da yarinya haka kamar wata bazawara, shi dai saurarenshi ba har suka shiga masallaci dan gabatar da abinda ya tarasu, Abdul na kallo aka nemi waliyanshi da kuma waliyin Raihan wanda Abbas ya nuna Bashir, saida aka gama d'aura aure akan sadaki dubu d'ari aka shafa fatiha Abdul ya mik'e tsaye yace "Kuyi hak'uri iyayena, auren nan da kuka d'aura yanzun nan zan warware shi, dan ba zan uya zama da fasik'a ba, kamar yanda ba zan iya kiran wad'anda bansan meye nufinsu ba na had'a ni aure da 'yarsu ba a matsayin srukaina ba, dan haka *na saki Raihan saki uku*, idan ta samu miji ko yanzu ma tayi aurenta." Kallonshi duk mutane cikin masallacin sukayi yayin da kawunshi ya mik'e ya ci kwalar rigarshi yace "Kai Abdul meye haka? Baka da hankali ne? Ya zamu d'aura maka aure yanzu yanzun nan kawai ka saki yarinya? Akan wane dalili?" Abdul kallon Abbas yayi wanda shi ko d'ago kai baiyi ba saboda yanda yaji abun har tsakar kanshi, yarshi Raihan, ita ce ya d'aurawa aure yanzu kuma aka saketa a gabanshi? Lallai rayuwar nan abar tsoro ce, kallon kawunshi yayi yace "Kawu ina da dalili na, ba haka kawai nayi abin nan ba." Yayan Safeena mahaifiya Abdul d'in ne yace "Dalilin k'aniyarka, koma menene dalilinka saika saketa daga d'aura muku auren, dama soyayyar k'arya kake mata?" "A'a kawu, soyayyata gareta ba k'arya bace, sai dai su ne bansan wace irin soyayya suke min ba da har zasu lullub'e min kura da fatar akuya su ban a matsayin mata wacce zata zama uwar 'ya'yana." Abba ne ya taso daga inda yake zaune yana tattare balaluwarsa, yana zuwa ya kife Abdul da mari yace "Kai butulun ina ne? Wato ka gado a wajen mahaifinka ko? Ni dama da yaron nan yabi ta tawa da bai had'a jininshi da jinin wannan macucin ba, shine yanzu daga d'aura aure a tsakiyar masallaci zaka saki yarinya, kenan nufinka dama ka mayar da ita k'aramar bazawara?" D'agowa Abbas yayi danya takawa Abba birki kafin allura ta tono garma, suna kallon juna ya mishi alama da dan Allah Abba kayi shiru, Abba daya fahimta fita yayi daga masallacin. Sunkuyawa yayi kusan Abbas da har yanzu kanshi ke k'asa yace "Na d'auke ka kamar mahaifina, ina girmamaka, duk da nasan mahaifina ya cutar da kai, amma meyasa zaka rama a kaina? Meyasa zaka aura min Raihan bayan kasan wacece ita? Meyasa kayi gaggawar tsayar da ranar auren mu? Bayan kaga wannan ne?" Ya tambayeshi yana nuna mishi hotunan Raihan, a hankali Abbas ya kalli hotunan take ya d'auke kanshi, Bashir dake kusa da shi ne ya fizgo wayar yana fad'in "Meye wannan d'in? Wane sakarci n..." Bai k'arasa ba shima saboda ganin hoton Raihan tsirara, da sauri ya d'auke kanshi ya jefa mishi wayar, Abdul kuma na karb'ar wayar kawunshi dake tsaye bayanshi ya nuna ma yace "Kawu ganin wannan hotunan ne yasa uncle Abbas saurin aura min yarinyar, bayan haka kuma wai ni har gwajin jini suka min bada sani na ba saboda basu so na aureta ace ina da wata cutar wanda mahaifina ya d'auko ya sakawa mahaifiyata." Shiru sukayi sai yan maganganu k'asa k'asa yayin da Abbas ya kalleshi yana mamakin inda yaji batun gwajin jinin kuma, suna zaune haka da d'aya d'aya mutanen cikin masallacin suka fece suka bar daga Abbas sai Naseer da Bashir da kuma liman da abokin Abbas d'in nan, abokin kasuwancin Abbas d'in ne mai sunan *Alhaji Khamis Abbas* ya dafa kafad'ar shi da niyyar rarrashinshi, amma zuciya tasa Abbas tashi da k'arfi ya bar masallacin, kai tsaye gida ya nufo kuma ta falonshi ya wuce d'akin Sameera, Sameera na gama shiryawa tana rufe wadrob d'in ta ta juyo ta kalli Raihan dake kwance tana baccin wahala, zata fita kenan Abbas ya shigo d'akin da k'arfi wanda yasa gaban Sameera fad'uwa dan yanayin shi zai nuna maka ba lafiya ba, wajen Raihan ya nufa dake bacci yana zuwa iya k'arfin shi yasa ya mata wani bugun tsiya a baya, da k'arfi ta farka tare da ihu da kuma wani tarin wahala, kafin ta tashi zaune ya finciko dogon gashinta ya jawota k'asa yana shirin fita da ita daga d'akin, da gudu Sameera ta k'arasa ta durk'ushe ta rik'e ta tana rufe mata jikinta, dan dukan da taci ranar yasa bras kad'ai take iya zama da ita sai wani dogon wando wanda bai kamata jikinta ba, kallonshi tayi ido jawur cikin b'acin rai dan abun ya fara isarta tace "Abban Ameer meye haka wai? Ya zaka mayar min da yarinya kamar wata jaka? Me tayi maka?" Sakin gashinta yayi ya nunasu da hannu yace "Ni yarinyar nan zata kunyata ta tozarta a idon al'umma? Kinsan meya faru yanzu? To auren da aka d'aura mata yanzun nan Abdul ya saketa saki uku saboda ganin hoton shaid'ancin da take aikatawa a waje, me zan mata idan ban illata ta ba?" Kallon fuskarta Sameera tayi ta kuma kalleshi tace "Abdul d'in ne ya saketa? Wane hoto kuma?" Cikin b'acin rai ya fito da wayarshi ya nuno hoton ya nuna mata, tana gani ta lumshe ido tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Raihan? 'Yar dana haifa?" Kallonta data mata yasa Raihan ganin ta sake shiga uku, da sauri ta mik'e tayi baya nesa da su cikin matsanancin kika tana fad'in "Iyayena dan Allah ku fahimce ni, wallahi ban aikata abinda kuke tunani, idan baku yarda ba zaku iya kaini duk likitar da kuke so a duba ni." A fusace Abbas yayi kanta ganin haka Sameera da sauri ta mik'e ta shiga tsakaninsu tace "Kayi hak'uri dan Allah ka nutsu, idan muka bi ta zuciya zamu iya kasheta, a k'arshe zamu iya yin nadama." Yatsa ya nuno mata ya bud'a baki zaiyi magana wayar shi tayi k'ara, juyawa yayi ya koma inda Sameera ta saki wayar ta taso ya duba, lambar Alhaji Khamis ne wanda suke mutumta juna, juyawa kawai yayi ya fita daga d'akin inda Sameera ta juyo kan Raihan ta wanketa da mari tace "Mamana abinda zaki saka min dashi kenan? Me na miki a rayuwa da kika zab'i hukuntani ta wannan hanyar?" Dafe kunci tayi tana kuka zata durk'usa k'asa ta fizgota ta nufi toilet da ita, suna shiga ta mayar da k'ofar ta rufe ta kama Raihan da k'arfi ta zage mata dogon wandon had'e da pant d'in ta, kunya ce tasa Raihan ja baya tana rufe gabanta, wata harara Sameera ta wurga mata hakan yasa ta d'an kawar da kanta, ba zato ba tammani taji wani zafi ya ratsata da k'arfi sakamakon shigar da yatsa da Sameera tayi na kusa da manuniya, k'ara tayi lokaci d'aya kuma tayi shiru har wasu hawayen wahala sun zubo mata, fito da yatsan tayi ta kalleta sai kuma ta zauna dab'as a tsakiyar toilet d'in, ita gaba d'aya ma kanta ya kulle ta rasa taya zata iya fahimtar yarinyarta budurwa ce, ba zata iya kaita likita ba gaskiya saboda sanannun mutane ne su, hakan zai tab'a kima da kuma mutuncinsu, Raihan kuma d'aukar wandon tayi ta mayar ta sunkuya tace "Ammie, dan Allah ki daina kuka a kaina, Ammie zan sake samu wani mijin na aura, nayi miki alk'awari da idonki sai kin tabbatar da yarki bata watsar da tarbiyyarta da kika bata ba." A waje kuma yana fita Alhaji Khamis ya samu k'ofar masallacin ya tsaya, cikin nutsuwa Alhaji Khamis yace "Alhaji Abbas na fahimci duk abubuwan dake faruwa, idan zaka bani dama zan so na karb'awa babban d'ana *Baban gida* aurenta? Dan bai kamata a fasa d'aura auren nan ba." Kallonshi Abbas yayi sosai, hak'ik'a yasan Alhaji Khamis mutumin kirki ne mai sanin ya kamata da dattako, sai dai kuma baisan komai a game da d'an sa ba, duk lalacewar Raihan kuwa zai yarda yayi wannan gangancin? Ganin baice komai ba yasa Alhaji Khamis cewa "Nasan abune mai wahala, amma karka damu ka fad'a min abinda ke ranka, maganar aure tafi k'arfin wasa, Baban gidan bai tab'a aure ba, karatu ya saka a gaba, yanzu haka ma yana *Maroc* wurin karatu, amma shekara mai zuwa zai kammala ya dawo gida, sunan mahaifina ne da shi, wato takwaranka ne." Kallonshi Abbas yayi sai kawai yace "Ba damuwa Alhaji Khamis, ai hallaci ka mana, kasan yarana ka haifesu amma baka haifi halinsu ba." Take suka shiga masallacin yan mutanen da suka rage suka shaida d'aurin auren *Abbas Khamis Abbas* da kuma *Khadija (Raihan) Abbas Abdul rahaman* akan sadaki dubu d'ari biyu. Suna fitowa daga masallaci ana taya juna murna suna tattauna yanda tariyar zata kasance, amma Abbas cewa yayi ai kawai tunda shi Khamis gobe ne zai tafi to kawai zai tafi tare da surukarshi, sannan a yau zai gama mata shirye shirye taje can ta samu mijinta, kuma duk yayi hakane dan ya kawar da ita daga gabanshi, dan ranshi b'acewa yake idan ya ganta kuma tana tuna mishi da abinda shi ma ya aikata, nan Alhaji Khamis ya kira gida ya sanar da iyalai, mahaifiyar Baban gida ta rasu sai kishiyoyi, hakan yasa babu wacce tayi murna da jin haka, dan su abinda suka hango ba wai dalilin auren da gaggawa ba, a'a, tarin dukiyar da mahaifin yarinyar ke da shi, mutumin daya mallaki jirage na kanshi, compagnie da masana'antu ba adadi, sannan uwarta ma jinin sarauta ce, wannan bak'in cikin yasa suka kasa farin ciki, saidai sunyi abincin sadaka kamar yanda mai gidan yace, dan in basuyi ba rai zai b'ace kasancewarshi mutum jajirtattace a gidanshi. Baban gida ma da yaji musu yayi wa mahaifin nashi, amma dayake yana da zafi saiya balbaleshi da bala'i yace idan ya turo mishi yarinyar ya yankata idan ya cika d'an halak ne shi, haka yaja baki yayi shiru shima yana jiran isowar yarinyar. *Ma'aruf* da kanshi ne ya shigo musu da abun kari, babu abinda Ma'arufa tayi tunani dan dama kusan kullum shi ke siyowa, ko da baya da kud'i ita zata bayar ya siyo, yana kallonta har ta gama cin indomie ta d'auki lemun daya siyo mai sanyi ta fita dashi tana sha, fatan alkairi ya mata har da cewa tayi sauri ta dawo fa, tana kan hanyar zuwa ta kira Abbas a lokacin an d'aura auren yana wa su Ammie bayani, ganin lambarta yasa shi barin waje ya d'anyi nesa da su, Harira data fito d'auke da jus jus d'in da zata kaiwa bak'in dake gidan ta ganshi yana amsa waya, tsayawa tayi ta lab'e ta kasa kunne tana sauraren shi. Abinda taji kawai shine "Naji, mu had'u a inda muka had'u jiya, amma ki sani wannan uta ce had'uwarmu ta k'arshe dake." Tana ganin ya nufi wajen ajiyar motoci ta d'an fito daga lab'ewarda tayi ta aje jus jus d'in ta rigashi fita, yana fitowa ya d'auki hanya ita ma cikin sa'a adaidaita ta fito daga kwana, shiga tayi tace su bi bayan motar... 👏👏👏 22/06/2020 à 17:26 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _21_ "Dan ubanka meye haka? Wallahi idan ka sake dukanta saina rama mata tunda d'an iska ne kai, Ammar meye haka? Zalincin ne ya motsa maka? Wannan wane irin haukane da iskanci? Me yarinyar nan ta maka da zaka kamata da duka haka?" Cikin d'aga murya kamar zai fasa gidan yace "Ummy inba raini da iskanci ba ni Amna zata rainawa hankali? Na d'auke na kaita shagon Ilu amma dan iskanci a gabana zata tsaya kula wani bayan kuma tasan nine mijinta, akan me zata min haka? Laifin me nayi? Tana so ta nuna ni ba cikakken namiji bane ko me? Waccen d'in da me ya fini? Kyau? Ilimi ko kud'i? Ko kuma lafiya da girman jiki taga ya fini?" Cikin hassala Ummy tace "Mijinta? An d'aura maka auren da ita ne? Kai bari ma na tambayeka? Ka k'addara an d'aura muku auren, kenan haka zaka mata wannan dukan tana matsayin matar taka?" Zaro ido yayi yace "To me zan mata? D'aki zan sakata na dinga rera mata wak'a ina mata rawa dan na kwantar mata da hankali?" Kallonshi Ummy tayi tace "In kuwa hakane lallai ba namiji bane kai, ba zaka tab'a zama jarumin namiji a gurin mace mai hankalin da tasan ciwon kanta, tun ranar da aka ce Amna ce k'addarar aurenka ta fad'a mata na fara mata kukan tausayi, dan indai har akayi kuskuren had'a ta da kai to babu makawa yarinyar nan tana daf da ajalinta." Take yaji wasu hawaye na son taho mishi, mahaifiyarshi ce data haifeshi take fad'a masa haka? K'ok'ari yayi ya mayar da hawayen ya kalli Amna yace "Kina ji ko? A dalilinki ne take fad'a min haka, ni kuma nayi alk'awari saina tabbatar muku da namiji ne ni." Girgiza kai Ummy tayi ta kama Amna suka mik'e tana gyara doguwar rigarta, Husseina ce da mamaki ya isheta tace "Amna kuma? Ai ba Amna bace Hamna ce, Ammar meyasa baka tsaya kayi tunani ba kawai ka hau dukanta haka?" Dafe k'ugu yayi da hannu d'aya hannu d'aya kuma ya nuna kanshi yace "Kenan yanzu na zama mahaukaci ne da ban iya gane yaran da har goyasu nayi a bayana? Yaran da suka tashi a gaban idona ne zan kasa fahimtar wacece wannan ko wacce waccen?" Kallonta Ummy tayi dan ta gane wacece ma a ciki, sai dai duhun dake akwai wajen bai bari ta iya ganewa ba, hakan yasa tace "Da gaske ne? Amna ce?" Gyad'a kai tayi alamar eh, sallalami Husseina ta fara ta rik'e baki tace "Oh ni Husseina, yanzu dama Amna ce nake wa kallon Hamna? Amma meyasa dana kira Hamna kika amsa? Ita tana ina?" Amna da har yanzu take jin marin nan daya mata da takalmi kuka kawai ta sake fashewa dashi, shi kuma k'wafa yayi ya kalleta ya nunata yace "Daga yanzu duk inda zaki je saina baki izini indai har nine wanda zai aure ki." wucewa yayi inda Ummy ta bishi da kallo ganin jikinshi biji-biji ga kayanshi sai k'yallin mai suke, kama Amna tayi suka shiga ciki bata yarda sun tsaya falon ba, sama suka haura d'akin su suka zaunar da ita, fad'a Ummy keyi sosai na haushi da takaici, har da cewa "To ubanki ne shi da har zaki tsaya ya miki wannan dukan? Ba dan kin zama sakarya ba ma akan me zakiyi tsaye yana d'irkarki haka? Amna aure fa ake shirin yi miki dashi, da hakane zaku zauna kinsa tsoronsa a ranki? Na tabbata da yer uwarki ce Hamna wallahi ko gudu ne tayi daga gurinshi, dan baya da maraba da mahaukaci idan ranshi ya b'ace." Amna dai shiru tayi sai sharar hawaye take, hakan yasa Ummy cewa "Kiji harda wani cewa wai in zaki fita saida izininshi, to mu duk aikin banza ne kenan a gidan? To zaki fita bada izinin nashi ba sai naga in kasheki zaiyi." D'agowa Amna tayi cikin kuka tace "A'a Ummy, tunda dai yace haka ni zan bi umarninshi, zan nemi izininshi kafin na fita, shikenan sai a zauna lafiya, ko Mama ma tana fad'a mana mu dinga jin maganarshi dan shi kad'ai ne ke tsawatar mana." Da mamaki Ummy tace "Ke yanzu sai ki biye masa kuma?" Jinjina kai tayi alamar eh tare da cewa "Ummy hakan shine zaman lafiya na, nasan ni ba yer uwata Hamna bace, nice mafad'aciyar kuma mai zuciyar, amma akan yah Ammar bana da ko d'aya, bansan meyasa ba." Tab'e baki Ummy tayi tace "Lallai kina da aiki Amna." Ko da yayi wanka shiryawa yayi cikin riga da wando bak'ak'e, makullin mota ya d'auka ya sake fita, k'aramin gurin cin abinci ne *Kebab* ya zauna ya ci abinci, daga nan kuma hanya ya d'auka saida ya samu inda babu hayaniya ya paka nan, jingina kawai yayi yana sauraron wa'azindake tashi a motar, maganganun Ummy ne kawai ke dawo masa a k'wak'walwa, awa d'aya da rabi ya d'auka a wurin nan kamar mai bacci kafin wayarshi ta fara ruri, saida kiran ya tsinke aka sake maidowa kad'ai ya taso daga kwanciyar da yayi ya d'auki wayar, a zuciyarshi yace "Abdullahi kuma? Meyasa zai kirani a wannan lokacin?" Tsaki yayi saboda wata zuciyar data fad'a masa watak'ila zai maka k'orafine saboda baka je d'aukar amarya ba, d'auka yayi ya d'ora a kunne yayi shiru, daga can b'angaren Abdullahi yace "Ammar yane? Kana cikin gari ko kana gida?" Can k'asan mak'oshi yace "Lafiya?" Abdullahi ne yace "Lafiya ba lafiya, dama a cikin yan matan amarya ne aka bar wasu basu samu komawa tare da sauran mutane ba, kuma gashi duk wanda na kira wallahi wasu ma sun fad'a min kai tsaye ba zasu iya dawowa d'aukar su, ni ma kuma mota ta tun safe tana hannun k'ane na, yanzu haka nafi awa d'aya ina jiran adaidaita sahu ko taxi na samar musu amma wallahi shiru, gashi dare na k'arayi shiyasa nace bara na kiraka dan Allah ka zo ko Hamna ka d'auka, tunda kaga gidanku ba bari fitar dare ake yi ba inba da dalili mai..." Ammar ne ya dakatar dashi cikin sanyayyar murya yace "Ya isa haka dan Allah, magana ba tsayawa ba numfasawa, yanzu kenan nufinka naje na zama drebata na d'auko ta? Bayan kuma a gida babu wanda ma yasan da fitarta, to ba zan iya ba." Abdullahi ne yace "Dan Allah Ammar ka taimaka, bana so ne ta shiga matsala a dalilin halartar bikin nan nawa, dan Allah." Tsaki yayi ya kashe wayar, hakan kuma yasa Abdullahi yarda d'ari bisa d'ari cewa zai zo, dan haka ya ci gaba da tsayuwa a bakin titin, ai kuwa baifi minti ashirin ba saiga motar Ammar, dan dama yasan gidan da jimawa dan anjima ana ma gidan tsare tsare tsare da tanadi, k'arasawa sukayi k'ofar gidan Abdullahiya shiga ya samu su Hamna cirko cirko su biyar a farfajiyar gidan, Hamna ya kalla yace "Hamna ki taso ga Ammar nan zai tafi dake." "Wa!? Ta fad'a da k'arfi tana zaro ido ta d'ora da "Waya fad'a mishi ina nan? Meyasa sai yanzu ya zo bayan ban ganshi d'azu ba?" Abdullahi ne yace "Yanzu dai ba lokacin magana bane ki taso ku tafi kafin ya mana tijara ni dake." Mik'ewa tayi tace "Ina zuwa." Cikin d'akin ta shiga ta samu amaryar tare da babbar yayarta tana k'ara gyara mata d'aki, uwar d'aki suka shiga Hamna tace "Dan Allah k'awata taimako zaki min." "Taimakon me kuma k'awata?" Cikin fargaba tace "Yah Ammar ne ya zo d'auka ta, kuma jiya ma a wurin kamun ku saida ya min fad'a kan fita babu hijabi, shine nake so dan Allah ki ara min ko da babban mayafi ne, insha Allahu gobe idan na taso daga école zan biyo na kawo miki." Murmushi tayi ta nuna mata wurin kayan tace "Besty akan wannan ne har kike cewa wani taimako? Ki duba ga kayan nan sai ki zab'a." "Yawwa." Ta fad'a tana bud'a wurin kayan, wani babban mayafi ta d'auka wanda ya dace da kayan nata, ita kanta data kalli madubi sai taga tafi kyau da kamala, sai ta ganta kamar wata amaryar ita ma, fitowa tayi zata fita sauran k'awayen suka ce ai ba zata barsu ba, tare suka fito inda ta zagaya zata shiga motar, da kallo ya bita har ta shigo, amma take jikinshi ya bashi wannan ba mayafinta bane, cikin lallami Abdullahi ya zuro kai yace "Abokina ka taimaka ka aje wad'annan ma mana, in kayi haka zaka samu lada fa." Kallonshi yayi fuskar nan a d'aure yace "Me zai hana ka basu makwanci a gidan naka? Ai sabgaka suka zo? Ni munyi da kai zan zo d'aukar maka mata ne?" Murmushi Abdullahi yayi yace "Ba haka bane, amma dai ka taimaka." Mayar da kallonshi yayi kan titi yace "Kasan zasu rage maka jin dad'i kenan? Shine ni ma zaka takura min." Kallon yan matan yayi da suka saki baki suna kallonshi yace "Ku muje." Da sauri wuka bud'a suka shiga suka zauna, ko kallon Abdullahi baiyi ba ya ja suka wuce, saida sukayi tafiya mai nisa babu mai magana kafin ya daidaita madubin gabanshi yana k'arewa yan matan kallo, a ranshi yake k'yamar irin shigarsu kamar ba yaran musulmi ba, babu wacce babu k'arin gashi a kanta da muguwar kwalliya ta d'aukar hankali, girgiza kai yayi ya juya ya kalli Hamna, sai kace wata malama k'wafa yayi ya ci gaba da tuk'i, sunyi nisa muryar d'aya daga cikin yan matan tace "K'awa Hamna da kina da yaya kyakyawa haka shine bamu sani ba?" Wani buhun haushi ne ya tasowa Hamna, tasan halin k'awarta dan haka ta d'aure fuska ta kalli Ammar da yake tunanin kalar iskancin da zai tatawa yarinyar, tab'e baki tayi a zuciyarta tace "Wai kyakyakwa, humm." Ammar kuma juyawa yayi zai kalli k'awarta ta sai kuma ya ga ita sai wani had'e fuska take, kallon gabanshi yayi hakan yasa k'awar cewa " Yayanmu mun gode fa daka d'auko mu, dan har mun fara tunanin k'aryar da zamu fad'a a gida zuwa gobe." Cike da shak'iyanci yace "Karki damu, ai mace irinki tafi k'arfin ta rasa mai sa'ar da zai d'auko ta, ni ne da godiya." Fasa mata kai yayi da wannan maganar tashi, sai kawai tace "Nagode, amma nima sa'ata ce ace na shiga motarka har muna musayar yawu da kai." Tsaki sukaji wanda yasa shi kallon Hamna da tayi tsakin, to na meye? Haka kawai taji ranta na b'acewa sai kumbura take, kamar Ammar yasan me take ji a zuciyarta sai kuwa ya biyewa k'awar suna ta hira, saida aka kawo inda zasu sauka tace "Mai kyau zaka iya aje ni anan ma." Da murmushi yace "To mai kyau." Pakawa yayi su biyu suka sauka ya zuro kanshi yace "Bansan nawa ne farashin lambar wayarki ba, amma zan so ki fad'a min komai tsadarta zan biya dan a bani." Cike da duniyanci tace "Farashinta mai tsadar gaske ne, amma kai na musamman ne, dan haka kawo wayarka na saka maka kyauta." Cikin fara'a ya mik'o mata wayar yace "Ina godiya da wannan karamcin." Tana cikin saka masa tace "Ai karrama mai karamci yafi k'arfin iyawata ni kad'ai, kai babban mutum ne." Saida ya saci kallon Hamna yayi murmushi yace "Kinsan ba kowa yake gane girma da darajarka ba, wasu idan sukaga suna rayuwa tare da kai sai su mayar da kai kamar abun banza." Bashi wayar tayi ya amsa tana fad'in "Ka rabu da su kawai, zasu fahimta ne a sannu duk ranar daka mallaki wacce zata dinga nuna musu darajar taka." Wani murmushi yayi na iskanci yana goge lambar yayin da ita kuma take tunanin yana saka lambar ne a wayarshi yace "Ke wasu fa mahaukata ne basa fahimta duk yanda zakiyi da su, ki barsu da shan kayan ruwa kawai suna cika musu mafitsara." Dariya tayi sosai yayin da sauran kuma sukaji kunya, kamar tasan da Hamna yake sai cewa tayi "Barta kawai, zan dinga fahimtar da ita matsayinka ko ta fara ganin girmanka." Ammar ne yace "Amma zan iya sanin adadin matakan tsaron dake gidanku? Domin idan na tashi zuwa nasan irin shirin da zanyi." Murmushi ta masa tace "Ka zo duk sanda kake so, zaka samu k'ofa a bud'e." Da wani yanayin shegantaka yace "Allah ko?" Ita ma a salon wayewa ta marmad'a masa ido, hannu ya zuro ya bata da niyyar su gaisa yana fad'in "Saina kiraki mai kyau." Bashi hannu tayi wanda yasha akaihu zargama zargama ita ma suka gaisa tace "Sai na jika mai kyau." Kashe mata ido yayi ba tare daya saki hannunta ba yace "Za dai ki jini a waya mai kyau, amma jina ai sai bayan aure." Murmushi tayi harda sunkuyar da kai tana d'an matsa hannunshi mai laushin gaske tace "Har kasa na fara tunanin kaina a matsayin matarka." Kallon wannan mahaukaciya ce ya mata yace "Ni fa tunda na ganki nake jin ina k'amshin lalle." Cikin b'acin rai da jin kamar ta rufe shi da duka tace "Dan Allah ni muje ka kaini gida na gaji da jin wannan zancen na ku." Juyowa yayi ya mata wani kallon zan ma ci ubanki ne yarinya, kawar da kai tayi shi kuma ya saki hannun k'awar ta ta yana fad'in "Saida safe." Jan motar yayi suka wuce har saida ya aje sauran ma kafin suka d'auki hanyar gida, babu mai magana ko kallon wani har suka kusa isa gida, a daidai su sha kwana motar police ke nan da alama wucewa zasuyi motar ta samu matsala, haka kawai wani police ya tsayar dasu, tsayawa yayi ya sauke madubin motar yana kallonshi daga shi har shi kowa fuska babu annuri, police d'in ne yace a harshen fransanci " Malam daga ina haka a daren nan?" A hankali Ammar ya kalli agogon hannunshi k'irar gucci ta fata, ganin duka yanzu ne k'arfe *11:18* na dare yasa ya kalleshi yace "Daga inda ka aike mu mana." Da alamar tambaya police d'in yace "Me? Malam wace irin amsa ce haka? Tambayarka muke daga ina kake?" "Amsar kenan na baka, akan me zaka tare ni yanzu kana tambayata daga ina nake?" Hassala yayi yace "Wai waye kai da zaka ce ba za'a tambayeka ba? Kafi k'arfin doka ne ko me? To fito daga motar sannan ka bamu takardun motar." Murmushi yi wanda har yasa Hamna tsorata dan tasan k'aramin aiki ne yayi bala'i da shi yasa su kwana a gark'ame, murfin motar ya kama zai fito yana fad'in "Bara na fito kaga tsawo na to." Cak ya tsaya saboda hannunshi da Hamna ta rik'e, yana kallonta ya ga hawaye har sun cika idonta, cikin rawar murya tace "Dan Allah ka basu takardun mu wuce." Fizge hannunshi yayi yace "Sake ni dallah, ni zai nunawa wannan k'azamin kakin nashi, waye shi da har zai tambaye ni waye ni? Bari na nuna masa daidai nake da shi, uban wa ma ya bashi damar tsayawa nan d'in." Zai fito ta sake rik'e rigarshi hawaye suka zubo mata tace "Dan Allah fa nace yah Ammar, ina jin tsoro." Da k'arfi ya kawar da kanshi daga kallonta saboda jin zafin ganin hawayenta da yayi, police d'in dake tsaye ne yace "Kai nake jira ai ka fito, madame ki barshi mana naga me zaiyi, naji kana fad'in wai k'azamin kaki na, to fito na nuna maka k'arfin ikon kakin nawa." Cikin hassala da k'ufula ya daki sitiyarin motar da k'arfi, yana son ya fita ya nuna mishi bai tsoronshi sai dai ya kulleshi, amma kuma baya son ganin Hamna cikin damuwar nan, ganin hawayen ta ma yasa shi jin babu dad'i haka yasa shi dole ya juyo ya kalle shi ya saisaita nutsuwarsa ya k'ak'aro murmushin na ganeka kuma zamu had'u ya masa yace "Yallab'ai, ka barmu mu tafi mana, madame d'in nan rigima ce da ita, kasan mace mai ciki saurin hawa." Jin haka sai police d'in ya k'ara jin wata izza ai sai yace "Kawai ka fito daga motar ka bamu takardunka, yo har mu zaka d'auka wasu sakarkaru har kake fad'a mana magana, yau zaka gani." Kallon Hamna yayi ita ma ta mishi kallon taimaka ka basu dan Allah, hakan yasa yace mata "Akwai takardun, amma wallahi ba zan bashi ba." D'aya daga cikin wanda suke tare ne yana duba motar ya matso yace "Ya dai? Lafiya?" Kafin police d'in yayi magana Ammar yace "Abokina wannan mutumin ne ke son b'ata min lokaci, to wai halan baya da aure ne? Inba haka ba ai da zai fahimci larurar da kan iya saka miji fitowa a dare kuma tare da iyalinshi, ka ganta nan." Ya fad'a yana nuna mishi Hamna da gabanta fad'uwa yake ido taf da hawaye ya ci gaba da cewa "Tun sallah isha'i ta sani zagaye garin nan da neman wani wai karas, na fad'a mata yanzu ba lokacin karas bane amma ta k'i yarda, kai har karas d'in da Allah ya hore min na ce ta gatsa ☹️ amma tace bai mata ba, da k'yar na samu yanzu na lallab'a ta ita da d'an baba na siya mata alewa zamu koma gida, yanzu gashi kasa min ita kuka, domin Allah haka ya dace?" Jami'in da yaga Ammar daban ne da mamaki yace "Dan Allah me sunanka?" Murmushi ya masa yace "Ammar, Ammar Hassan Gaga." Zaro ido yayi ya bashi hannu yace "Abokina kace yan biyun lieutenant ne? Ah masha Allah, zaku iya tafiya kawai, Allah ya tsare Allah ya raba lafiya." Hannu ya bashi suka gaisa kafin ya kalli waccen yana hararenshi suka wuce, suna tafiya ya kalleta ya mata rank'washin tsiya a kai yana fad'in "Shegiya yanzu baga anfanin saka babban mayafi ba, da wannan shegen siririn ne a jikinki da yanzu tayaya zan iya kallonki na ce matat..." Sai kuma yayi shiru, turo baki tayi gaba ba tace komai ba har suka isa gida, saida suka tsaya sun fito a tare suka nufi hanyar b'angaren su, tana daf da shiga falon ta juyo ta kalleshi tace "Allah ya isa rank'washi na da kayi." Juyowa yayi hakan yasa ta arta a guje tayi falon, girgiza kai yayi a ranshi yace "Ai zamu had'u ne, zan miki horon da har ki mutu ba zaki manta dani ba." Tana shiga falon ta tsaya das saboda Hajia data samu zaune kan kujerarta fuskarta a had'e sai kuma Ummy da Zeinabu gefenta da alama fad'a ta musu ke take musu, ko kuma dai tuhumarsu take, cikin tsananin fad'uwar gaba da sanyin jikin ta tako zuwa tsakiyar falon, murya k'asa k'asa tace "Assalama alaikum." Kallonta kawai sukayi amma babu wanda ya amsa, nufa hanyar da zata sada su da d'akin su tayi, a hankali Hajia tace "Zo nan." Kamar wacce k'waiya fashe ma a ciki haka ta taho ta durk'usa gabanta kanta k'asa, tsaye Hajia ta mik'e hakan kuma baisa Hamna yunk'urin kare kanta ba dan bata san Hajia da saurin hannu ba inba abu ya kai mak'ura ba, bata ankara ba taji saukar yatsu biyar, tana dafe kunci ta d'ago ta kalleta yayin da Hajia kuma tace "Ke har ni zaki mayar wata mahaukaciya a gidan nan, ina cikin gidan nan amma kike nema kiyi rayuwar da kika ga dama, me kike so ki zama Hamna? Yar iska? So kike ki zama kamar uwarki kenan? To baki isa ba wallahi, yanzu fad'a min a cikinsu wacece tasan da fitarki a gidan nan?" Ta fad'a tana nuna su Ummy, Hamna kuma babu abinda ya mata zafi kamar cewa wai tana so ta zama yar iska kamar uwarta, kenan mahaifiyar tasu ce yar iska? Lallai ni na jawa mahaifiyarmu wannan wulak'ancin, tsawa Hajia ta mata tace "Dake nake magana kina jina." Kallonsu Ummy tayi ta girgiza kai tace "Basu san fita ta ba." Cikin masifa tace "To gidan ubanwa kika je? Me kika je yi da baki dawo ba sai yanzu? Hamna kina 'ya mace ace ba kya cikin gidanku kina waje, to me kikeyi? Kuma ba a motonku kika fita ba, kenan wani ne ya zo ya d'auke ki kuma ya dawo dake." Kallonta Hamna tayi tace "Wallahi Hajia adaidaita na shiga, kuma wurin kan amarya ne muka tafi, nasan idan na tambaya ba za'a barni ba shiyasa, kuma ki tambayi yah Ammar kiji tare ma muka dawo yanzun." Kallonsu Ummy tayi tace "Ku b'ace min da gani ku Allah ya taimake ku." Tashi sukayi inda ita kuma ta koma ta zauna tana kallonta tace "Tare da Ammar?" Kai ta gyad'a alamar eh, amma me Hajia za tace sai cewa tayi "To na sani ko tare dashi kuke yawon iskancin na ku, dan ni ban yarda dake ba, shi kuma dama idonshi tsakar kai suke ba kunya ne dashi ba, yanzu idan na kira shi zai iya fad'a min abinda ya faru tsakanin ke da shi." Mamaki ne yasa Hamna kallon Hajia kawai ta kasa cewa komai, hakan yasa Hajia cewa "Je kirawo min shi, dan wallahi ko iskanci kuke yau saina kawo k'arshen shi a gidan nan, watak'ila dama wannan dalilin ne yasa kika k'i amince da auren nan." Mik'ewa tayi ta fita jiki a sanyaye da tunanin halin kakarsu, tana zuwa k'ofar d'akin ta tsaya dan tana jin hayaniyarsu, sallama tayi Amar ya amsa, ba tare data shiga ba tace "Yah Amar Hajia ke son ganin yah Ammar yanzu." Amar ne ya amsa da "Yana d'aki bari na fad'a masa." Juyawa tayi ta fita shi kuma ya shiga ya fad'awa Ammar, fitowa yayi babu ko riga zai fita Junaid yace "Haka kuma za'a tafi wurin Hajiar?" Ko kallonshi baiyi ba yace "To ko nine Hassan meye a ciki? Ba haihuwarmu tayi ba? Tunda ita ko dare da Allah yasa mana mu samu nutsuwa a cikinshi bata bari mu nutsun ai sai mu fara zuwa mata tsirara inta neme mu." Jibril dai da abun duniya ya isheshi da kallo kawai ya bishi, ai kuwa yana shiga Hajia ta kalleshi da wani mamaki, zaune yayi kujerar dake kallonta ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya wanda hakan yasa suke iya ganin kwantaccen gashin k'afar shi mai silb'i, ido cikin ido ya kalli Hajiar yace "Mutan makka gani, ance kina kira na yanzu a daren nan, shine nace bara na zo da gaggawa kar azo ko zuciyar ce ta fara bugawa ba daidai ba." A murtuke ta kalleshi tace "Duk maitarka wallahi zuciyata tafi k'arfin ka nuna k'warewarka a kanta, shege kenan burinka kenan a kai na." Murmushi ya mata na shegantaka yace "To in kuwa hakane baki shawara mana? Ki rage b'acin rai da sakawa mutane idanu, ki dinga samun isashen bacci hakan zaisa ki dinga samun nutsuwa, sannan ki rage yawon surutu da hayaniya, inba haka ba Allah in kika bari zuciyarki ta kamu da ciwo da hannu na zan parkaki na fito da zuciyar na 'yar da ita." Murmushi Hamna tayi harda rufe baki inda Hajia ta gama cika, cikin fad'a tace "To yanzu wace rashin d'a'ar ceta saka shigo min falo babu riga?" Murmushi ya mata yasa hannu ya shafi k'irjin shi har zuwa kan nonon shi yace "To dan kin kalli wannan meye? Ko jariri dai ba zai iya tsotsar wannan ba, kuma ma Hajajju me kike tsammani dama ga marar mata wanda yayi shirin kwanciya." Tsaki tayi yayin da Hamna ta sunkuyar da kai kamar tace k'asa bud'e na shiga, tana mamakin wannan rashin kunya tashi ita kam, a nutse ta kalleshi tace "Wannan take fad'a min wai tare kuka shigo yanzu daga wajen kan amarya, shine nake so naji daga bakinka?" Kallon Hamna yayi wacce ita ma ta kalleshi, murmushi yayi mata wanda ta tabbatar na mugunta ne, sai yanzu ta tuna Allah ya isar data masa, take tace "Na shiga uku." Kallon Hajia yayi yana murmushi yace "... *Addu'arku*👏 23/06/2020 à 13:57 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _22_ Murmushi yayi yace "Ni kuma? A ina muka had'u? Ni ina zuwa wannan shirmen banzan ne da har zamu had'u dake? Hajajju ki matseta ta fad'a miki inda ta tafi, amma ni karki tambaye ni, saida safenku." Mik'ewa yayi kam ya nufi k'ofa zai fita, juyowa yayi ya kalli Hamna wacce ta juyo ita ma tana kallonshi kamar ta d'ura mishi ashar, wata 'yar iskar shoki ya kwaso daga k'asa yayi sama da hannu ya rufe rabin fuskarshi yana dariya, haushi ne ya k'ara kashe Hamna wato irin yanda take yi masa ne yayi, kashe mata ido d'aya yayi ya fice daga falon, Hajia kuma kallon Hamna tayi tace "Wallahi idan kika sake fita daga gidan nan ba da izini na ba wallahi dake za'a d'aura auren nan, tashi ki bani wuri." Mik'ewa tayi jiki a sanyaye ta nufi d'akin su ita ma Hajia nata d'akin ta shiga, tana shiga ta samu Amna kwance kan gado da rabin fuskarta harya kumbura ga jini daya kwanta a idonta d'aya, kaya ta fara cirewa inda Amna ta mik'e tace "Yawwa kin dawo, Hamna gaskiya daga yau ba zan sake taimakonki ba idan kina son fita a gidan nan, ki nemi izini idan an barki ki fita amma ni ba zan sake amsa sunanki ba idan ba kya nan." Juyowa tayi da niyyar sauke mata kwadon bala'i sai kuma taga fuskarta a kumbure, da sauri ta matso ta zauna kusanta tace "Amna meya sameki a fuska haka? Ba dai dukanki sukayi ba?" Cikin b'acin rai tace "Eh mana duka na yayi, ki duba kiga yanda ya rugurguza min fuska kamar wata jaka." Da mamaki tace "Waya dake ki haka?" A k'ufule tace " Wa fa idan ba boss ba." Kwance tayi saboda tafasar da zuciyarta keyi ita kuma shiru tayi ta mik'e ta ci gaba da cire kayanta, ban d'aki ta nufa tana fad'in "Wallahi saina d'aukar miki fansa, ba dai ya dake ki ba, bak'in mugu kawai azzalumi." Tab'e baki tayi a ranta tace "Ga ki gashi ai idan ke ma kina son ganin fuskarki kamar ni d'in ne." *Washe gari* da safe Hajia na zaune a falo sai Husseina gefenta amma babu mai kallon wani, Hajia ce cikin yamutsar fuska tace "Ki fad'awa jikanki daga yau zuwa gobe ina son fara had'a kayan auren jikokina, dan haka ina so naga yayi bajinta ta hanyar kashe kud'i sosai, dan Jamila yar dangi ce mai nasaba da asali na k'warai." Murmushi Husseina tayi tace "Gashi kuma anyi sa'a mahaifin Jibril ya tara masa dukiya, kuma shi kanshi ma zai iya d'aukar nauyin duk wani caji da zaki mishi akan auren jikarki, dan haka karki damu kanki indai akan matsalar kud'i, akwaisu kuma za'a kashe ko nawa ne." Tab'e baki tayi ta harareta ta ci gaba da danna wayarta, Ummy ta fito a shirye zata tafi wurin aiki, sunkuyawa tayi wurin Hajia ta gaisheta, amsa mata tayi ta juya zata fita tace "Auren mijinki za ayi gobe, bai kamata ace kin d'auki hutun aiki ba?" Tsayawa tayi ta kalleta sai dai kuma bata da abun fad'a, idan ma tace ta bayar da uzuri zata ce ai asibitin tasu ce, dan haka Ummy ta girgiza kai alamar to ta juya jiki a sanyaye zata koma d'aki kuma ta sake cewa "Yau zuwa gobe yaranku su had'a min akwatinansu, sannan babu maganar dangantaka ko alak'a, komai ina so naga anyi na bajinta yanda zai nuna harkar manya." Ummy da Zeinabu ne suka jinjina kai daga inda suke tsaye kafin Ummy ta koma d'aki, Hamna ce ta fito tare da Amna cikin shirinsu na makaranta, gaishe da Hajia sukayi suka nufi k'ofa, suna fita Hamna ta fito da powder ta ruwa daga jakarta ta matsa a hannunta sosai, kallon Amna tayi tace "Ki fitar da moton ina zuwa." "Ina zaki je?" Cewar Amna, komai ba tace mata ba tana kallo ta nufi b'angaren su Ammar, ita ma bayanta tabi dan nemo izini wajen boss, suna kusan kaiwa Amar ya fito daga d'akin shigarshi sam bata bambamta data Ammar ba, sai dai kuma fuskarshi babu annuri a tare da ita, gashi ya saka farin gilashi a ido wanda yasa ya k'ara fitowa sak Ammar, Hamna na ganin haka tayi murmushin mugunta ta tunkareshi da sauri ta sanda kanta k'asa ta fara lalube lalube a jakarta kamar mai neman wani abu, da gangan ta kaiwa Amar karo tare da saka hannayenta bibbiyu ta damk'o rigarshi tana sakin yar k'ara alamar bata lura ba, kallon juna sukayi ta kalli rigarshi da powder ta fito a rigar mai hasken sararin samaniya, ido ta zaro alamar tsorata tasa hannayen ta matsa kusa dashi ta fara kakkab'e mishi amma a zahiri k'ara damuk'a rigar take tana fad'in "Wayyo Allah na boss kayi hak'uri, kayi hak'uri dan Allah ban kula ba ko kad'an, wai ni a ina ma na samu dattin nan?" Ta tambayi kanta tana kallon hannayen nata, Amar da ido kawai ya zuba mata kasa magana yayi sai karantar fuskarta da yake, ganin kallon da yake mata yasa ta ja baya ta fara tattare siket d'inta, yana lura da haka yayi saurin cewa "Karki bawa kanki wahala, ga boss d'in can." Ya fad'a yana nuna mata Ammar dake bayansu jikin motarshi tsaye duk yana kallon abinda ke faruwa ya rumgume hannayen shi a k'irji, a hankali ya taso ya fara takowa ya zuba hannayenshi cikin aljihun wandonshi yana tunkarosu, tana ganin haka da gudun tsiya hijabin daya tilasta mata sakawa yana tashi sama shima ta fita a gidan har tana bangaje mai gadi, da kallo ya bita inda Amar ya bita da dariya, kallon Ammar yayi yace "Allah ya isa wallahi, akwai muguntar daka mata wacce tasa ta rama a kaina." Tab'e baki yayi ya mayar da kallonshi kan Amna yana fad'in "Kai ka siya da kud'in ka, ni nace kayi shiga irin tawa?" K'wafa Amar yayi ya juya ya koma ciki dan sake shiri, Ammar kuma matsowa yayi kusan Amna wacce tayi saurin cewa "Ina kwana yah Ammar." Ba tare daya d'auke idonshi daga kan fuskarta ba yace "Izinin fita ne kika zo nema?" Da tsoro fal a idonta ta jinjina masa kai alamar eh, matsowa ya sake yi daf da ita ya zuro hannayenshi ya shafi gefen fuskarta inda ya kumbura, bud'a ijiyarta yayi yaga yanda tayi ja sosai, kallon fuskarta yayi yace "Kan ki yana ciwo ne?" Girgiza mishi kai tayi kafin ya d'ora da "Ki daina b'ata min rai kinji ko, ba son raina bane na daki mace, amma kinga wannan banzan ko yanzu da zan ganshi saina kikkifar dashi." Jinjina kai kawai tayi hakan yasa shi kama hannunta yace "Muje yau da kaina zan kaiki makaranta, ki rabu da waccen kankanar." Tsoro ne ya bayyana a fuskarta dan ita a yanzu kam bata fatan sake fita tare da shi, juyowa yayi ya kalleta yana ganin yanayinta ya had'e girar sama da k'asa yace " Meye? Ba kya so na kaiki ne? Ko mamaki kike? To ki saba ma dan in akayi aurenmu da kin samu ciki ba zan bari kiyi tuk'i da kanki ba, dan ni ba sakarai bane nasha wahala na d'auki tsawon awanni na zuk'urk'ula miki ciki amma cikin minti d'aya ki zubar, ba zai yiwu ba." Hannu tasa ta rufe baki ita dai tana kallonshi har ya bud'e motar ya zaunar da ita, rufewa yayi ya juya ta bishi da kallo, ga mamakinta sai gani tayi kuma ya nufi falon Hajia, gyara zama tayi dan tasan sai wanda ya ga fitowarshi, da shigarshi kamar yanda ya saba babu sallama, d'akin Ummy ya nufa yana kallon Hajia ya d'aga mata hannu yace "Hajajju barka da zama." Kallonshi tayi da harara tace "Wai kai wane irin kunnen k'ashi ne da kai? Na fad'a maka indai wannan yar iskar gaisuwar ce bana so ka daina." Murmushi ya mata yace " Me yasa kika k'i fahimtar ina son fara jin muryarki ne a kowace safiya kafin ta kowa?" Da mamaki ta kalleshi tace "Ina masifa ko?" Murmushin ashe kin fahimta ya mata yace " To ai ita ma d'in kyau take miki ko?" "Ita masifar?" Ta fad'a tana zaro ido, shiru kawai ya mata nufi d'akin Ummy, da sauri Hajia tace "Kai." Tsaye yayi amma bai juyo ba dan ya k'osa da maganar fa shi, ganin bai ko kalleta ba yasa tace "Uban waye zai siya min tv ta daka fasa jiya?" Juyowa yayi ya saka hannu d'aya a aljihu yace "Ki ce kawai na siyo miki tvnki amma ba ki tambayeni wa zai siya ba, idan fa nace lieutenant ne zai siyo miki sai kuma kice nayi rashin kunya?" Yana fad'a ya juya cikin takon k'arfi ya bud'a d'akin Ummy ya shiga ba tare da sallama ba, Ummy dake tsaye gaban madubi tana gyara dogon gashinta juyowa tayi cikin tsoro, tana ganinshi ta sauke ajiyar zuciya ta juya tana fad'in "Dama waye inba kai ba, ko Kamal kafin ya shigo d'akin nan sai yayi sallama ya nemi izinin shigowa an lamunce mishi, amma banda kai." Kujerun dake farkon shigowa d'akin na roba mai gautsi masu kyau ya zauna a tsakiyar yana kallonta, kafin yayi magana tace "Bai kamata ba ma na b'ata yawun baki na, dan haka kamar a addininka ne aka koya maka shi, ko kuma dai matsalar da kake da ne a k'wak'walwarka tayi tasiri har a sallamarka." Wani d'an iska ya furzar yana sake had'e fuskarshi ya kalleta yace "Ummy zamu iya yin magana?" Juyowa tayi tana murmushi ta zauna kan kujerar gaban madubin tace "Ina kwana Baba Ammar, fatan dai ka tashi lafiya?" Ba tare daya kalleta ba ya d'an k'ikk'ifta idonshi alamar fa ya gaji da zancen nan, shirun da yayi yasa Ummy sanin ba fa zai iya gaisheta ba kenan, girgiza kai tayi tace "Kafin nan muyi magana akan kayan lefenku, ya kamata ku fito da kud'i dan had'a lefenku, Hajia na buk'atar shi yau zuwa gobe." Had'e hannayenshi yayi yana mammatsawa yace "Ba damuwa, zanyi." A kauce ta kalleshi jin yace wani wai zanyi, ko me zaiyi? Oho! Banza tayi dashi kawai dan babu anfanin b'ata yawun bakinta a kanshi a yanda take gani, kallon fuskarta yayi yace "Ummy, dan Allah meye tsakaninki da Abba da har zai miki kishiya? Kishiyar ma kuma wai wannan yarinyar wanda ba komai had'a ki da ita zai ja miki ba sai zubar da aji." Kallonshi ita ma tayi tace "Na d'auka angama maganar nan, meye kuma na taso da ita? Kaga bana son tashin hankalin, aure ne za'a d'aura shi gobe, banda matsala da hakan, mahaifinka ya auri ko mace uku ce ma ya kawosu duk a goben, ni dai ina son zaman k'ark'ashin kulawarshi, dan haka wannan ba matsalarka bace." A tsanake ya kalleta yace "Ummy, ki fad'a min idan akwai laifin da kika masa? Ni zan masa magana ya fahimta, amma bai kamata ya miki kishiya ba a yanzu." Nuna shi tayi da hannu a zafafe tace "Kaga, ni dai a sani na ban masa wani laifi ba, ka daina maganar nan kawai idan ba so kake a fitar da uwarka ba a lokacin da za'a shigowa da mahaifinku amaryarsa ba." Mik'ewa yayi yana mayar da hannayenshi aljihu ya kalleta yace "Ummy tambaya nayi kawai ko akwai wani laifin da kika masa ne, dan ni a gani na a shekarun da kuka d'auka tare bai kamata ace kishiya ta biyo bayan haka ba." Tsaye ta mik'e ta nuna mishi k'ofa tace "Fitar min a d'aki na, kaje kayi duk abinda zakayi, amma ka sani wallahi idan ka ja min magana ba zan yafe maka ba, mutumin banza kawai, ni ce marainiyarka kenan zaka zo ka tsareni da maganar ko na masa laifi, idan ma na masa laifin saina zauna na fad'a maka? Ni kenan bansan ta yanda zan iya ji da matsalarmu ba har sai sakarai irinka ne zai mana magani, shi kaje ka tambayeshi mana idan kai marar kunya ne." D'aya hannunshi ya fito da shi ya kama yalwatattar k'asumbarshi yana shafawa, takowa yayi kusanta yana kallon idonta babu wani d'ar ko tsoro cikin taushin murya yace "Ummy, ko zaki iya tuna abinda ya faru muna da shekara goma sha shida a duniya ni da Amar? Mun samu matsala dashi akan riga, a lokacin Amar nada rigima sosai, ko abu nawa ne saiya nuna nashi ne ko yana son shi saboda yasan kowa zai goya masa baya, asalin rigar tawa ce, kuma ke ma kinsan haka saboda kinga alamar da nama tawa, amma sai kika rufe ido dake da duk sauran mutanen gidan kuka ce dole sai dai ni na hak'ura tunda nine babba, hakan ne yasa nima raina ya b'ace a cikin dare na yaga duka rigunan da reza, amma me zai faru? Washe gari Hajia ta mareni a fuskata ta zageni zagin da ko kare tayi wa saiya zubar da hawaye, ta kira ni d'an iska har ba adadi, ta kira ni shege munafiki mai bak'ar zuciya..." Sunkuyar da kai yayi yasa yatsa d'aya yana share hawayenshi, ba tare daya d'ago ba yace "Zagin da yafi tsaya min a rai shine data kalle ni a gabanki a gaban idon mahaifina ta kira ni da *d'an Allah bani*, wai da tasan haka zan zama da ko da aka haifeni tasa an min allurar mutuwa, a wannan ranar ta fad'a ni, ni Ammar nine *annobar ahalinta*, zuciya nayi na fita farfajiyar gidan ina kuka, na wuni a wuri d'aya zaune da tunanin ko zan samu wanda zai zo ya rarrashe ni ya kwantar min da hankali, amma babu wanda ya zo kusa da ni, a lokacin mahaifiyata ce kawai nake ganin zata iya zuwa kusa dani kuma ta rarrasheni, ganin ke baki zo ba yasa ni naje har d'akin ki, Ummy me kikayi a lokacin?" "Ina shiga kika rufe ni da wani fad'an wai na fita na baki wuri, haka kema kika sake kirana d'an iska mai ja miki magana, a k'arshe bud'a baki ki kayi kika ce wai na fice miki daga nan ba kya son gani na ko kad'an, Ummy kinsan meya hana ni barin gidan nan a wannan ranar?" Ummy dake kallon yanda hawaye ke zuba a idonshi kasa amsa mishi tayi, dafe k'irjin shi yayi saitin zuciyarshi ya ci gaba yayi da cewa "Ummy *saboda soyayyarki ne*, ina ji a jikina kamar idan na tafi na barki a gidan Hajia zata ci gaba da k'untata miki, hakan yasa na hak'ura na zauna duk da zafin da nake ji a zuciyata, bayan faruwar hakan kwana shida na d'auka ina zuwa d'akin ki da nufin gaishe ki, amma sai kika ce ko amincin da nake nema miki ba kya so bare kuma gaisuwa ta, daga ranar ne ya zamana duk d'akin da zan shiga a gidan nan bana iya sallama, Ummy zan fara gaishe ki ranar da kika fara kallona kamar d'an da kika haifa, zanje wajen Abba." Yana fad'a ya juya ya fita da sauri sosai, fad'awa tayi kan gado dab'as kamar an turata, sai dai ta nemi hawaye ta rasa, maganganunshi ke dawo mata, kenan babu abinda yake mantawa? Zai fara gashe ni ranar dana fara kallonshi *kamar d'a*, kamar d'a? Ba ma d'ana ba? Tunawa da tayi yace zaije wajen lieutenant kuma tasan ba lallai su kwashe lafiya ba, dan haka ta mik'e ta d'auki wayarta ta fara kiran lieutenant, amma bai d'aga ba saboda wayar na silence yana ganawa da wasu manyan mutane, aje wayar tayi ta fito falo sam bata wani saka wani al'amarin a kai ba bare tayi tunanin halin da d'an nata ke ciki. Yana fitowa ya samu Amna ta gaji da jiranshi, Hamna kuma ta d'auki moton ta tafiyarta, yana shiga taga ya had'a kanshi da sitiyarin motar yana sauke wata k'akk'arfar ajiyar zuciya, ya kusan minti biyar kafin ya d'ago ya jawo lotus d'in dake cikin motar ya goge fuskarshi da kyau, tayar da motar yayi suka fita daga gidan, saida suka fara tafiya ya kalleta wacce ita ma take kallonshi ganin sabon yanayi a tare dashi yace "Kinyi latti ko?" Ganin idonshi jawur alamar kuka ba wai b'acin rai ba yasa saida gabanta ya fad'i, duk sai taji jikinta yayi sanyi tana son sanin meye damuwar, cikin taushin murya tace "Yah Ammar lafiya? Me yake faruwa?" Kallonta yayi yana doka wani uban murmushi ya kuma kalli gabanshi ya ci gaba da tuk'i, har ta fidda ran zai mata magana sai kuma ta ji cikin wani yanayi dake nuna damuwar dake zuciyar mutum yana sakin murmushi yace "Amna meyasa zaki tambayeni me yake faruwa? Shin baki tab'a lura da abinda ke faruwa bane?" Girgiza mishi kai tayi hakan yasa ya kalleta yace "Tunda kike a gidan nan kin tab'a jin wani Ammar Allah yayi maka albarka? Ko kuma zan fita kiji wani yace Allah ya tsare ko a dawo lafiya? Ko kuma kiji ance Allah ya taimake ka ko makamantan haka?" Shiru tayi alamar zurfafa tunani da sauri yace "Karki ba kanki wahala, ba zaki tuna ba dan babu ranar." Ci gaba yayi da tuk'i harya sauketa, har zata shiga cikin makarantar yace "Ko na zo na rakaki ne? Kin makara fa sosai." Cikin sanyin jiki tace "A'a yah Ammar, kaje kawai, kai ma nasan ka makara a asibiti." Jinjina kai yayi alamar to ya fara k'ok'arin tayar da motar, kamar daga sama ko saukar ruwa ya tsinci muryar Amna cikin wani mugun yanayin da har k'asan zuciyarshi ta birgeshi tana fad'in "Allah ya kiyaye hanya yah Ammar, Allah ya baka abinda kaje nema, Allah ya tsare mana gabanka da bayanka, saika dawo." Tana fad'a ta d'aga masa hannu alamar bye bye ta shige ciki, da kallo ya bita yayin da yake jin wani farin ciki na nuk'urk'usar zuciyarshi, wani murmushi ya saki wanda shi kanshi ya manta rabon da yayi irinshi, ba tare daya daina murmushin ba ya ja mota sai asibiti. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Maryama da Iklima sun duk'ufa shirye shirye na gyaran jikinta da sauran abubuwan, kulawar da kakarta da kuma mahaifiyarta ke nuna mata kamar yanzu suka haifeta, haka ma Huda soyayya suke nunawa yarinyar sosai, wanda a yanzu Huda bata da aiki sai fad'in Abbanta Jibril wanda ya yanka mata saniya, yau ma asibiti suka shirya suka tafi aka cire mata robar da aka saka mata dan hana d'aukar ciki, a hanyarsu ta dawowa Iklima ke cewa "Yanzu Mari kin shirya haihuwa kenan da zaran kin shiga gidan?" Murmushi ta mata tace "To me zanyi idan ba haihuwar? Bana da budurcin da zaiga mutumci na da shi, nasan ina shiga gidan soyayyar da yake nuna min zata ragu, kinga kuwa kafin na fara fuskantar tasku k'wara ina shiga na fara dire masa 'ya'ya." "To amma meyasa ba zaki fad'a masa gaskiyar waye wannan d'an uwan nasa ba? Ina ga hakan zaifi." Murmushi ta sakeyi tace "Zan fad'a masa, amma bayan naje gidan." A hankali Iklima tace "To Allah yasa alkairi." ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Kawu Mamu ma tuni yaje rugagensu yayi shelar bikin Zeituna, wacce yanzu a gidan kamar sarauniya, wani lokacin kawu da kanshi ke kawo mata abinci har bukkarsu, wani lokacin ma idan akayi tuwo sai yace ba zata ci tuwo ba, da kanshi zai fita ya siyo mata tsire ko gasassar kaza ya kawo mata, Zeituna saidai tayi wanka ta sake kaya ta koma ta zauna kan katifar Jumare da yanzu kawu yace ta zama ta ta har a d'aura aure, yau dai kam kanta ya sake kullewa da taga yan uwa na zuwa wai gobe aurenta da lieutenant, jira kawai take taga goben tayi saita tabbatarwa da kanta, sai dai kuma ana haka kawu Mamu ya sanar da ita Alhaji yace anjima da dare lieutenant zai zo su gana, hakan yasa ta k'arasa wuninta da muguwar fargabar had'uwarta da lieutenant d'in. ➡️➡️➡️➡️➡️➡️➡️ Yana sauka daga aiki da rana kai tsaye douanes ya wuce, yana fitowa daga mota ya tunkari ofishin, saida wani yaron lieutenant yace masa yana ganawa da bak'i, amma saiya nuna mishi d'an shi ne kuma abune na gaggawa, yana shiga ofishin babu sallama ya same shi zaune tare da wasu manyan alhazzai biyu, tsaye yayi yana kallonshi inda lieutenant ya mik'e da mamakin rashin sallamarshi ko neman izinin shiga bare gaishe da mutanen, cikin jin haushi yace "Wai kai mahaukaci ina ne? Ya zaka shigo wuri babu izini babu gaishe da mutane ka wani yi mana tsaye? To uban wa kake bi bashi anan? Me ma ya kawo ka?" Kawar da kanshi yayi yana kallon mutanen da suma suke kallonshi, abun mamaki sai lieutenant yaga sun mik'e suna bawa Ammar hannu da fad'in "Likita, kaine anan? Ya kake ya aiki?" Ba fara'a ya amsa da "Alhamdulillah." D'ayan ne yace "Yallab'ai ko yaron wajenka ne?" Cikin ji kunyar amsawa ya d'an jinjina kai alamar eh, murmushi sukayi sai d'ayan da yace "Ko da nace, ashe likita gadon mutumci da kirki yayi tun daga gida, ai likita na ne dake duba ni, yana da son mutane wallahi da jansu a jiki indai aka ce majinyacinshi ne kai." Kallon lieutenant sukayi suka bashi hannu suka ce "Ba damuwa yallab'ai, zamu jiraku a waje harku gama, nasan abune mai mahimmanci ya kawo shi." Yana fad'a suka fita suka barsu, cikin jin haushi da halayarshi ya koma ya zauna yace "Meya kawo ka nan?" Ba tare daya zauna ba yace "Abba ina son sanin wani abu ne, na tambayi Ummy tace na zo na tambayeka, shiyasa na zo." Fuska a d'aure yace "Menene?" A tak'aice yace " Wani laifi Ummy tayi daka yarda zaka mata kishiya?" Da k'arfi ya buga teburin gabanshi ya mik'e yana fad'in "Shirmen banza! Dama abinda ya kawoka kenan? Uwarta ka ce ta turoka ka min wannan tambayar?" Fuska a murtuke yace "Babu ruwanta, kawai ina son sani ne, idan akwai laifin data maka ka fad'a min?" Nuna mishi k'ofa yayi yace "Banda lokacin wannan haukan naka, ka b'ace min da gani daga nan." Jinjina kai yayi yace "Shikenan na tafi." Fita yayi daga ofishin inda lieutenant ya zauna yana dafe kai, daga nan *transa mall* ya wuce dan sunyi magana da abokinshi d'aya daga cikin manyan mall d'in, yana zuwa akwatinan daya siya kawai aka saka mishi a boot ya biya kud'in, daga nan ma wajen masu goro ya nufa ya siyo kafin ya nufo gidan daf da la'asar. 👏👏👏 25/06/2020 à 11:27 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _14_ Wuyan rigarshi ta cakuma tana jijjigawa ba tare data daina wannan kururuwar ba, wayar hannun nata ta kwad'a mishi a kai ta sake cakumar rigarshi ta fara fad'in "Ni! Ni? Ni Abbas?" Rik'e hannayenta yayi ya fizgesu daga rigarshi ya sunkuya zai d'auki wayar data fad'i, ba zato ba tammani ta turashi kan gadon ya fad'a da k'arfi, ya kalleta da jin haushi zaiyi magana sai kuwa saukar mari katssssss, dafe kunci yayi da wani irin mamaki a fuskarshi na irin yaushe nayi lalacewar da har zaki mare...? Bai gama ma kanshi wannan tambayar ba yaji ta sake shak'ar wuyanshi tare da yin tsalle ta haye ruwan cikinshi ta shak'e mishi wuya sosai, a yanzu kam ya fahimci hankalinta baya tare da ita, hakan ne yasa shi rik'e hannayenta gam ya birkita da ita sai gashi kan ruwan cikinta yana k'are mata kallo ba tare daya saki hannayenta ba cikin d'aga murya yace "Meye haka? Me yake damunki ne? Baki da hankali ne?" Wani k'arfin tsiya ne ya zo mata wanda yasa ta ture shi daga kanta a dole ya sauka samanta ita ma ta taso da k'arfi tana fad'in "Ni ce ma bana..." Sai kuma ta kasa magana saboda yau zuciyar ta taso gaba d'aya, hannayenta ta kai zata sake shak'ar shi alamar fa ita ranshi take nema sai yayi saurin rik'e ta ya had'e hannayenta biyu ya matse ya jawo k'ugun ta ya had'a da nashi haka ma ya had'a goshinsu da hancinsu wuri d'aya, lumshe ido yayi yace "Shiiiiiiiiii, Sam, meya faru? Meya sameki ne? Ki nutsu ki fad'a min." Manyan manyan idonta ta sauke cikin nashi wanda suka mata jawur abun tsoro, bud'a baki tayi tana so tayi magana amma zuciya a wuya take, sai wata shashek'a ta dinga saukewa kamar tana fitar rai wanda hakan ya matuk'ar tsorata shi, k'irjin ta ya kalla wanda keyin sama da k'asa da k'arfi da kuma sauri, idonta sun k'ara fitowa waje sosai kamar dai mala'ikan d'aukar rai ne ke cire nata ran, da sauri ya zaunar da ita kan gadon ya durk'usa gabanta ya tallabo fuskarta ya d'ago kanta ya had'a bakinshi da nata, lumshe ido yayi a hankali ya shiga tsutsar bakinta har yayi nasarar kamo harshenta yana tsotsa, ita ma ruf ta rufe idonta saboda jin numfashinta na daidaituwa, saida taji komai ya fara saisaituwa shi kuma ya fara mata tsutsa dake nuna ya fara d'aukar caji har ya fara matsa na shanunta ya zura d'aya hannun a bayanta zai zare mata zip, bud'e ido tayi ta sauke a lumsassun idonshi, bai ankara ba ta kama leb'enshi na k'asa da iya k'arfinta ta datse hak'oranta ta cije shi, jin cizo a bazata yasa shi tureta da k'arfi ya mik'e yana mata wani kallo, mik'ewa tayi tana kallon idonshi da sukayi jawur saboda rad'ad'in cizon, giftashi tayi zata fita daga d'akin ya rik'o hannunta yace "Wai meye haka? Aljanu ne dake kome?" Kawar da kanta tayi na wucen gadi kuma ta kalleshi, a k'alla ta d'auki minti ashirin tana kallon k'wayar idonshi ta kasa d'aukewa tsabar mamaki da al'ajabi, shi ma kuma kallonta yake yanayinta na bashi tsoro, da k'yar ta iya nuna kanta tace "Ni Abbas? Ni zaka tozarta? Ni zaka ciwa mutumci? Abbas me nayi maka a rayuwa? Na gaza wajen nuna maka soyayya ne, ko kuma na gaza wajen gamsar da kai ne? Shin baka jin dad'in tarayya dani ne da har zaka kawo min karuwa gida na? A cikin gida na Abbas? A d'akin bak'i na?" Juyawa tayi zata fita ya rik'o ta tare da shan gabanta, zaiyi magana ta nuna shi da yatsa fuska a had'e a murtuke tace "Zaifi ka rufe bakinka, idan mun had'u a lahira a mana hisabi." Cikin takon k'arfi ta juya ta fita daga d'akin ya bita da kallo, dafe kai yayi ya zauna bakin gadon yana shafa kanshi, da sauri ya kalli wayar dake k'asa tare da d'aukar ta ya kunna, ganin wannan vidéon yasa ya jefar da wayar yasa hannu yana shafa gemunshi, ya d'auka abin yayi sauk'i amma sai yaji bud'o k'ofar daya sake hargitsa masa lissafi, mik'ewa yayi ya juya yana kallonta, ganin ta nufo kanshi da wuk'a a hannunta yasa shi saurin tunkararta yana neman rik'e hannayenta, da yake masifa take ji da bala'i saita zame tare da wawura mishi wuk'ar sai a damtse, cikin sautin wahala ya dafe wurin tare da juyowa gareta ya furta "Ashhhhhh." Ido cikin ido suka kalli juna ta masa murmushi tace "Wallahi da haka zan dinga yankan namanka har ka mutu, Abbas ni zaka wulak'anta." Tayi kanshi ya cabko hannun mai wuk'a ya murd'e sosai yasa d'aya hannun mai ciwo wanda jini ke zuba ya fizge wuk'ar, jefar da ita yayi ita ma ya cillata kan gado ya nuna ta da yatsa yana fad'in "Sameera ki saurare ni mana, ya zaki dinga abu kamar wata marar hankali? Kar kisa na ji miki ciwo a banza mana, shin zina a kaina aka fara? Ko kuma kin saurareni na fad'a miki abinda ya faru ne? Haka kawai zakkk..." Bai k'arasa ba ta mik'e da k'arfi tana girgiza kanta gashinta duk ya yamutse tasa hannayenta ta tura shi baya, bubbuga k'irjinta tayi cikin disashewar murya tace "Ni ce marar hankalin? Kai ne mahaukaci bani ba, kai da ka zubar da mutumcinka wajen k'aramar yarinya, kai ko kunya baka ji ko kunya ba? A cikin gidanka ka shigo da karuwa, shine harda k'aryar cewa wai ka bigeta ne a hanya shine ka taimake ta, kaji kun..." Wuyan rigarta daya finciko yasa ta yin shiru, saida ya kai bakinshi saitin nata bakin yace "Kisan me kike fad'a min Sameera, bana son maganar banza, ki zauna ki saurare ni." Ya k'arashe da sakinta yana nuna mata kan gadon ta zauna, fashewa tayi da dariya ta nufi wajen dressing miror d'in shi ta d'auki kwalbar turare mai kyau da tsadar gaske ta buga a madubin tace "Wai umarni kake bani? To ai yanzu ni bana ganinka da wani mutumci ko kad'an wallahi, kai Abbas ba..." Marin daya zabga mata a fuska yasa ta dafe kunci tana kallonshi, da yatsa ya sake nunata yace "Wallahi ni banyi lalacewar da har haukanki zai k'are a kaina ba, Sameera kisan ni mijinki ne bai kamata ki d'aga muryarki sama da tawa ba bare har ki dinga fad'a min duk shirmen da ya zo bakinki, tabbas ina sonki, amma son da nake miki ba shi zaisa na miki shiru ki ci mutumci na ba, wallahi tsaf zanyi k'asa k'asa dake a wurin nan, iskancin banza kawai, zuciya kanki farau, ko ke kad'ai ce me zuciya a k'irji? An fad'a miki kowa baya jin zafi ne? Wallahi ba dan tausayinki ba da rashin sabo a gare ni da dukan tsiya zan miki har ki dawo hankalinki, amma duk da haka zan iya hukuntaki ta hanyar data fi dacewa dake." Hannunta ya kamo da niyyar wurgata kan gadon sai kuwa ta d'auko wata kwalbar turare doguwa, cillata yayi kan gadon ya bi kanta ya haye yasa k'arfi ya b'arka rigarta rantsetsen leshenta wanda yaji kud'i da d'inki mai kyau, shi kanshi yayi mamakin yanda ya iya raba rigar biyu saboda kark'on leshin, zai fizge bras d'in ta yaji saukar kwalbar nan a kanshi wanda take jini ya sake gabce mishi a kai, gefenta ya fad'a ya dafe kai ya rufe ido sosai, mik'ewa tayi cikin k'arajin murya tace "Wallahi ka gama kusanta ta Abbas, indai ina raye ba zaka sake shigar da banzar..." Jin an shigo d'akin ne yasa ta shiru ta kalli k'ofar, Khalifa ne ya shigo wanda hayaniyar iyayen nashi da jin lallai ba lafiya ba yasa shi shigowa, a hankali ya tako har ya tsaya gabanta yana kallonta, a tsawace tace "Lafiya? Meya kawoka?" Juyawa yayi ya kalli Abbas daya d'ago ido d'aya ya kalli Khalifa, matsawa yayi kusanshi yace "Dady ciwo kaji?" D'auke hannunshi yayi wanda yasa jini sake gangarowa har yana neman rufe mishi ido ya mishi murmushi ya girgiza kai alamar a'a, juyawa yayi ya kalli Sameera dake k'ok'arin cire rigarta yace "Ammie meya samu Dady?" Tsayawa tayi daga shirin gyara rigar ta nuna mishi k'ofa tace "Dan ubanka fice min a d'akin nan kafi na ji maka ciwo." Wani kallo Abbas ya mata na mamaki, shi kanshi zai so Khalifa ya fita danya nuna mata shi ba sa'anta bane har yanzu, cikin sanyin jiki Khalifa ya juyo ya kalli Abbas yace "Dady dan Allah ku daina fad'a, duk gidan nan fa ana jin muryoyinku, mun saba ganin kuna rigima da fad'a, amma waccen fad'an naku yana saka mu nishad'i wani lokacin ya kuma bamu dariya, amma wannan ba kamar kullum ba, dan Allah Dady karka biyewa Ammie." Kanshi ya dafa zaiyi magana Sameera tace "Iyee! Khalifa ni zaka wa iskanci? Wato halin ubanka ne zaka d'auka ko? Shine ma zaka ba hak'uri ba ni ba? Kasan me yayi kuwa? Bara ka gani to." Jujjuyawa ta fara kamar mahaukaciya tana neman wayar nan, can ta hangeta kusa da k'ofar toilet inda Abbas ya cillata, da sauri ta d'auko ta bud'a vidéon nan zata tunkaro Khalifa tana fad'in "Dubi tsiyar da mahaifinkkk." Marin da Abbas ya wanka mata lafiyaye a kumatu yasa ta sakin wayar ta fad'i ta kaiwa k'ofar toilet d'in karo, a fusace yasa k'afa ya take mata k'afafu biyu ya juyo ya kalli Khalifa ya nuna mishi k'ofa yace "Fita anan, ka umarci k'annan ka ku je gidan Naseer." Jiki a sanyaye Khalifa ya nufi k'ofa yana kallon mahaifiyarshi dake yashe k'asa, saida ya kai k'ofa zai rufe yace "Dan Allah Dady k..." A tsawace Abbas yace "Ka fita nace." Da sauri ya rufe k'ofar sai hawaye, da gudu ya fita neman taimako gashi kuma Ammie bata nan, a k'ofar gida ya samu Abba ya sanar dashi babu lafiya a ciki fa, a sukwane suka taho tare... Yana ganin fitar Khalifa ya cakumi gashinta ta baya ya buga kanta da bangon wurin, hakan ya haddasa mata sakin k'ara mai k'arfi da sauri kuma ya sunkuya ya sa hannunshi ya rufe mata baki, da k'afa ya tura k'ofar ban d'akin ya sake cakumar gashinta ya jata cikin ban d'akin, yana zuwa k'aton bahon wankan dake cike da ruwa ya kinkimeta sai kuwa ji kake tamjam ya sakata ciki, da k'arfi ta yunk'uro tana neman tsira ya tausa kanta ciki, hannayenshi ta shiga k'ok'arin b'anb'arewa daya taushe mata kai, amma dayake Abbas yana son ya koya mata hankali ta gane shine gaba ba ita ba, a kullum tana tunk'aho da jiji da kanta da zuciyarta da jarumtarta, rufe ido yayi ya k'i sakinta yana kallon yanda take son ta fito ta numfasa, amma ya kawar da kai daga kallonta yana fad'in "Wai ba kasheni zakiyi ba? To ni zan fara kashe ki in ya so mu had'u a lahira a mana hisabin,." Kallonta yayi yace "Wai ni kam ba kece Sameera mai zuciya ba da d'aukar fansa? To ina zuciyar ta ki? Shin ba kece ba kya yafiya ba duk abinda aka miki sai kin rama? To gani ki rama mana, ki fito ki rama nace." Saida yaga ta galabaita sosai ya saketa ya juya zai fita daga toilet d'in, da k'arfi ta yunk'uro ta zuro kanta waje tana tarin wahala da kakarin amai, juyowa yayi yana kallonta wani tausayinta ya baibayeshi da tuna cewa fa shine mai laifin, dawowa yayi ya tallabota ya d'auko ta ya fito da ita har kan gado ya direta, kallon fuskarta yake yana gyara mata gashinta daya had'e wuri d'aya yana zubar da ruwa, tallabo fuskarta yayi yana kallon cikin idonta cike da rarrashi yace "Dan Allah Meerah ki kwantar da hankalinki muyi magana, ni da ke yan uwan juna ne kuma miji da mata, ki bani had'in kai mana mu fahimci junanmu, shin kina ganin wannan abinda kike har kina so ki kashe shine mafita? Sam, zaki iya rayuwa ba tare da ni ba?" Yanda ya kafeta da ido ya nuna amsa yake jira, da wani wahalallen kallo ta kalleshi da manyan idonta wanda suka canza gaba d'aya sai lumshewa suke, cikin hard'ewar hak'ora ta bud'a baki tace "Kashe ka yanzu shine kawai mafita, dan inba gawarka na gani ba hankali na ba zai kwanta ba, idan ba gani nayi ka daina numfashi ba ba zan tab'a farin ciki ba, Abbas dole ka mutu, dan ba zan iya ci gaba da zama da kai ba, to akan me ma zan zauna da kai? Ni b'ata shekaru ina killace maka kaina, sai kawai na wayi gari naga hoton iskancinka kai da wata, watan ma kuma har cikin gidan da yake mallakina, Abbas ni zaka rainawa hankali da wata banzar k'aryarka ka shigo min da karuwarka har gida, gaban iyayenka da yaranka da kuma ni, ni Abbas? To me kake so nayi idan ba kashe ka ba?" Girgiza kai yayi yace "Yanzu kenan ba zaki saurare ni ba, shin kinsan ma wacece wannan yarinyar? Meerah daga had'uwar mu da ita har abinda ya faru tsakaninmu duk shiri ne, shine da suka shirya dan ruguza mana rayuwa, shiri ne dan tarwatsa rayuwata da kuma taki data yaranmu, idan kin tuna fa washe garin ranar da abun nan ya faru aka nemeta aka rasa, shin kinsan nawa ta nema a hannu na tana blackmailn d'ina? Ki farka daga bacci Sam, idan ba haka ba sunyi nasara a kanmu a karo na biyu." Mik'ewa tayi tace "Ban damu nasan wacece ita ba, abinda na sani kawai shine ita ce wacce ta kwanta da mijin da nake ganin kamar nawa ne ni kad'ai, Abbas a tunani na na d'auka ko aure kayi matarka ta sunna zakaji kunyar kwanciya da ita a gidan nan, saboda ina tunanin kana so na kuma na gama maka komai ta yanda zakaji kunyar kusantar wata mace, ashe ba haka bane, da karuwa ma zaka iya wulak'anta ni, ashe kasan abinda kake aikatawa kenan shiyasa ka d'aga hankalinka daga ganin hoton Raihan wanda ita nata mai sauk'i ne ma akan naka, haka ka dinga shirgar min 'ya kamar ka samu jakarka duk dan kana tsoron kar tayi abinda kayi, kasa mun aurar da ita a gaggauce ko mak'wabtanmu ba duka suka san da aurenta ba kamar wata marar gata, ka had'a ta da wanda baka san halinshi ba kuma tayi nesa damu, duk dan kana so ka b'oye laifinka." Juyowa yayi zaiyi magana a lokacin su Abba suka shigo a hargitse, tsayawa sukayi suna kallonsu da mamaki, Abba ne ya iya cewa "Abbas lafiya? Me yake faruwa ne haka?" Murmushi Abbas yayi ya d'an dafe ciwonka da duk taji mishi yace "Ba komai Abba, kawai dai..." Shiru yayi hakan yasa Sameera mik'ewa ta kalli Abba tace "Abba ba gaskiya bane, baya so ya fad'a ne saboda abun kunyar daya aikata ba k'arami bane, amma ni zan fad'a maka." Matsowa ta sake yi inda Abba da Khalifa suke kallonta da ido, Abbas kuma matsowa yayi kusanta yana so ta bud'a bakin zatayi magana ya dakatar, dan ba zai lamunci ta fad'i abin nan ba a gaban d'an shi na cikin shi, sam ba zai jura ba ko da hakan na nufin ya mata dukan da zai sumar da ita ne, kallon idon Abba tayi ta kalli Abbas tace "... 👏👏👏 25/06/2020 à 11:27 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *SANIN MASOYI* _(sai Allah)_ *BAYA DA K'URA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 💞 _*MASOYA NA*_💕 _Bismillahir rahamanir rahim_ 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _13_ Yana isa ya sameta a ciki tsaye bakin wata bishiya da lemu a hannunta tana sha, inda Harira ke binshi cikin iya takonka ba tare daya sani ba, yana zuwa ya tattare babbar rigarshi kamar zaiyi dambe da ita cikin fad'a yace " Meye kuma yanzu? Meyasa kika ce na zo nan? Ko kin manta da na biyaki kud'in da kika nema?" Kallonshi tayi tana murmushi tace "Dady..." Yanda ya nunata da yatsa yasa tayi shiru, ido ya zaro mata yace "Karki sake bakinki ya sake kirana da ubanki, ni ba ubanki bane." Ita dai murmushi take kafin ta fito da wayarta ta rik'e a hannu tana jujjuyata tace "Ok, dama nace ka zo mu had'u ne saboda wani tunani da nayi, na fahimci waccen farashin nayi maka sauk'i sosai, shiyasa yanzu na zo dan na fad'a maka ina buk'atar wasu kud'in." Cikin b'acin rai da hassala ya shak'i wuyanta da duka hannayenshi biyu ya had'a ta da jikin bishiyar cikin d'aga murya yace "Me kike nufi? Me kike so ki mayar da ni? D'an iska ko me? To ba zan bayar ba, kije kiyi duk abinda zakiyi, abun kunya ba'a kaina aka fara ba." Ma'arufa da tunda ya shak'eta ta saki waya da jaka da lemun hannunta ta fara kakarin numfashi, sai dai a wannan d'an tsakanin kuma sai wani ciwon ciki daya taso mata na ajali, dafe cikinta tayi tana matsawa tana so ma tayi kuka da ihu amma Abbas ya shak'eta sosai, shi kuma duk a ganinshi wahalar shak'ar daya mata ce, ganin jini ya fito ta hancinta ne yasa shi sakinta sai kuma ta fad'i gabanshi, juya mata baya yayi yana huci da son saisaita nutsuwarsa suyi magana, juyowa yayi da k'arfi zaiyi magana sai kuma ya ga har yanzu bata tashi ba, baya ya ja yace "Ki mik'e, we need to talk." Shiru ko motsi ba tayi ba hakan yasa ya d'an sunkuya ya daddab'a kafad'arta yace "Dake nake magana." Shiru babu amsa daga Ma'arufa, turata ya d'an yi hakan yasa fuskarta ta fito tayi rairai tana kallon sama, ganin idonta a kakkafe bakinta bud'e daga yanda take neman numfashi ga kuma jini a hanci, tsoratar da yayi yasa shi wajen yayi baya da k'arfi harya fad'i zaune a wurin, tabbas gawa ce wannan, na kasheta ko me? Da sauri ya rarrafo ya fara jijjigata yana fad'in "Dan Allah Ma'arufa, karki mutua wannan halin kuma a hanu na, kar zunubin ya min yawa mana, please ki tashi Ma'arufa." A tak'aice ya d'auki minti talatin a wannan halin yana tausa k'irjin ta da nufin numfashinta ya dawo, amma shiru babu labari, haka kawai ya fara hawaye da sambatu barkatai yana ji kamar ya kashe kanshi, tunani ya shiga yi na mafita kafin daga bisani zuciyarshi ta yanke miki kawai ya jefar da gawarta, yana gamsuwa da haka ya mik'e ya cire balaluwarsa ya jefata cikin mota, sam ya manta da wayarta da kuma lemun da take sha, ita da jakarta kawai ya d'auka yasa a boot ya fizgi mota ya bar gidan gonar. Harira da har fitsari ya kusa sub'uce mata a wando saida taga fitarshi ta fito, idonta akan wayar tasa hannu ta d'auka, dama kuma Ma'arufa ba tsaro take sawa a wayar ba, tana ja sama taga ta bud'e kuma abun mamaki akan wannan banzan video ne wanda ita taga zahirinshi ma, tsaki tayi ta sunkuya zata aje wayar sai kuma tayi cak kamar an tsikareta, tsaye tayi tana kallon wuri d'aya tana tunani, wani murmushi tayi jin wani tunani daya zo mata, sai kawai tasa wayar a jakarta ta juya dan barin gidan. Ko da Ammie ta fad'awa Sameera d'aurin auren Raihan da wani tayi fad'a har bakinta ya fara kumfa, tana ganin kawai yana neman maraba da ita ne shiyasa ya had'ata da wanda bai san halayenshi ba, kuma wai yace gobe Alhaji Khamis zai tafi da ita Maradi, jibi kuma an gama mata visarta saita wuce Maroc, saida Abba tace tayi wa mutane shiru kad'ai taja baki tayi shiru tana gunguni. Tafiya yayi kamar zai bar gari duk inda ya gani sai yaga kamar za'a kama shi, kuma har wannan lokacin yana tunanin anya kuwa abinda zakayi daidai ne? Da k'yar ya isa wata doguwar hanya da babu mutane sosai, nan kawai zuciyarshi ta yanke mishi ya ajeta bakin titi ko ta samu taimako a mata sutura daga wasu bayin Allah, haka kuwa yayi saida ya tabbatar babu kowa ya fito da ita ya aje tare da jakarta da d'an kwalinta kafin ya juya ya bar wurin zuciyarshi cunkushe jikinshi na rawa na rashin saboda da tsintar kai cikin gagarumin tashin hankali, daga nan gida ya nufa da tunani iri iri. *Basraba* Gidan sarauta gaba d'aya ya hargitse da hidima na walima da aka shirya, sosai aka ci aka sha kafin yamma tayi aka fara shirin tarban amare kamar yanda uwar d'aki ta buk'ata, yamma tayi rana tayi sanyi gidan ya k'ara yamutsewa ta ko ina saboda bak'i da suka fara shigowa da amaren, nan hadimai da bayi suka fara kai da kawowa suna nuna musu masaukinsu, haka aka dinga shiga da amaren suna gaishe da uwar d'aki da kuma sauran matan da kuma uwar gidansu gimbiya Ameera kafin aka wuce dasu nasu masaukin. *A gurguje* Da dare bayan jakadu sun shirya Jawahir wacce ita ta fara isowa gidan kafin Safiyya, hakan kuma na nufin ita ce gaba da Safiyya yau ita ke da sarki, sarki ma da kanshi ya tarasu su ukun ya nuna musu mahimmanci da darajar uwar gidanshi, sannan ya nuna musu yana son zaman lafiya da kuma had'a kansu, yana gamawa ya sallami kowace ya koma bed d'in shi. Uwar d'aki da kanta ta turo jakadiyarta ta taimakawa sauran bayin aka shirya Jawahir cikin shiga ta alfarma kafin ta kamota har falon sarki tayi wa sarki magana sannan ta koma, izinin shiga ya mata bed d'in, cikin nutsuwa da jin kunya ta shiga kanta k'asa, kan gado ya nuna mata ta zauna shima ya zauna kusanta yana kallonta, ba laifi kam kyakyawa ce ga kuma kunya, saidai akwai k'ananan shekaru gareta da gani, ganin ta k'i d'agowa ta kalleshi yasa ya kalli hannayenta da suka sha lalle, sake kallonta yayi yace "Jawahir." Har zata d'ago kanta kuma saita tuna yana daf da ita dan haka ta k'i d'agowa ta amsa da "Na'a." Murmushi yayi dan ta birgeshi data kasa kallonshi hakan yasa ya mik'e ya kama hannunta yace "Muje muyi alwala muyi sallah." Mik'ewa tayi tabi bayanshi har toilet, saida ta d'aga ido ta kalli toilet d'in ganin ban d'aki kamar d'akin kwanan wani, tare sukayi alwala suka fito sukayi sallah, bayan sun kammala ne ya mata tambayoyi kan addininta musamman yanda zatayi wankan tsarki da kuma yanda take sallahrta, abun mamaki shine amsa wasu tambayoyin da tayi ba daidai ba, bai wani nuna mata k'yama ko wani abu ba sai kawai ya bar abun a ranshi da d'aura niyyar d'ora mata a hankali harta fahimta, a nutse ya kalleta yace "Kina buk'atar wani abu ne da zaki ci?" Kai ta girgiza alamar a'a, mik'ewa yayi tana kallo yayi shirin baccinshi tana zaune, ba zato ba tsammani taji ya kamo hannunta ya zaunar akan gadon ya koma ya kashe hasken d'akin sannan ya dawo, kwantar da ita yayi kamar wata beby ya kwanta gefenta, a hankali cikin nutsuwa da dabara ya samu ya lallab'a ta har ta zama cikakkiyar mace a wannan daren. Kamar yanda mahaifanta suka rad'a mata tun kafin auren hakane ta kasance, a lokacin daya shiga ban d'aki dan tsarkake jikinshi cike da k'arfin halin duk da bata iya wa haka ta mik'e ta ta saka kayanta tayi sauri ta yaye wannan zanin gadon ta tura k'ark'ashin gado sannan ta zauna bakin gadon, yana fitowa ya kalleta da mamaki ya k'araso yana fad'in "Jawahir, ya zaki takura kanki haka? Kije kiyi wanka kinji." Cike da dagiya ta murmusa kanta k'asa tace "Ba komai, dama zan canza zanin ne kuma bansan a ina zan samu ba, shiyasa..." Maganar ta tace ta sark'e haka kawai dan haka ya kamata ya nufi toilet da ita yana fad'in "Ki barshi kawai, ni zan canza wani da kaina, yanzu ki samu ki kula da kanki kinji ko." Yana fitowa ya fara k'ok'arin canza zanin, yana da niyyar idan ta fito ya tambayeta ina waccen zanin? Dan kar azo ta fita da shi sai kowa ya ga meya faru tunda akwai k'uruciya a tare da ita, amma jimawar da tayi tana kula da kanta da kuma kunyar fitowa yasa har bacci ya fara ridarshi saboda akwai gajiya a tare dashi, tana fitowa kuma jawota kawai yayi suka kwanta yana rumgume da ita a k'irjin shi kamar yar tsana. *Abuja* Cikin tsanani rud'u ya shigo gidan ya kuma zarce bed d'in shi, kile k'ofar yayi inda ya cire kayanshi ya shiga wanka, haka ya zauna ruwa na sauka a kanshi yana kuka kamar yaro k'arami, sam wunin ranar bai ma san ya akayi shi ba bare kuma yasan yanda ya gudanar da nashi, sanda Sameera ta ankara da motarshi taje d'akin dan suyi magana amma bai bud'e mata ba, haushi ne yasa ta baro k'ofar da niyyar ba zata sake komawa ba sai in ya fito dan kanshi, sam kamar ba gidan da aka d'aura aure ba, a haka har dare yayi yan mutanen da kenan ma suka watse, da dare kusan kowa ya kwanta amma banda Sameera dake tare da Raihan ana ta gyaran jiki, haka ma Abbas da abun duniya ya isheshi yake tunanin halin daya samu kanshi cikin d'an lokaci, sai kuma Harira data samu lambar Abbas d'in wurin Abdul raheem tana kwance kan k'aramin gadonta zata kira shi. Yana kwance yana kallon sama kiran Harira ya doki kunnuwanshi, har ga Allah saida gabanshi ya fad'i kuma ya zabura ya tashi zaune, dan yanzu fa ya zama marar gaskiya ne kowane kira d'aukar shi yake wata matsalar ce, k'ara shiga damuwa yayi ganin bak'uwar lamba, amma wannan karan sai yayi saurin d'auka saboda maganin matsalar bai tsaya b'ata lokaci ba, shine ya fara cewa "Wake magana?" Harira na jin muryarshi saida gabanta ita ma ya fad'i kafin ta daure tace "Harira ce." Da d'an k'arfi yace "What! Harira kuma? Wacece hakanan kuma?" Murmushi tayi tace "Harira dai yar k'auye mai aiki gidanka, na kira ne muyi magana idan kana da lokaci?" "Bana da to." Ya fad'a a harzuk'e, dariya tayi dan tasan maganar yayi ne cikin jin haushi sannan tace "Dama wayar siyarwa ce gareni mai matuk'ar tsada wacce nake ganin da kai kad'ai zata dace, amma tunda kace baka da lokaci shikenan, saida safe, amma karka manta da abinda masu iya magana ke fad'a, *ko a k'ark'ashin k'asa ka shiga ka aikata abu to ka sani akwai ranar da zai fito*, bare kuma kai da a bayyane kayi komai naka ma, ka sani yanzu bana ganinka da wani sauran mutumci, tun ranar da nayi mugun gani, yallab'ai Abbas da karuwa a cikin gidanshi ba kunya ba tsoron Allah, tirr." D'orawa tayi da "Ban tab'a tunanin zaka iya aikata zina ba, amma sai gashi naga ka aikata har kisan kai ma, hakan fa na nuna rashin imaninka yayi yawa." Abbas da rigarshi tayi sharkaf da gumi yaji kanshi ya fara juyawa jikinshi ya fara kyarma ba tsayawa komai yace "Ke kuma nawa kike so?" Wata dariyar jin dad'i tayi tace "Da idona naga duka ta'asar da kayi, a yanzu haka kuma ina rik'e da wayar yarinyar daka kashe mai d'auke da vidéon caskalenku, ni ba kud'i nake so sab'anin hankalinka ne, idan har kayi abinda nake so ni kuma zan rufa maka asiri har abada." "Ki fad'a min kawai me kike so da gaggawa? Sannan ki min alk'awarin zaki bani wayar nan idan har nayi abinda kike so." Saida ta gyara kwanciyarta kafin tace "Ina so ka aure ni, da ka amince ni kuma zan baka wayar tare da duka idanu na da sukaga abinda kayi." Sauka yayi daga kan gadon yace " In aureki? Ke a wa? Ke tsaya kiji, halin da nake ciki fa bai haukatar da ni ba ta yanda zan iya had'a kaina dake ba bare kuma har na had'a ki da matata, dan haka ki canza wata buk'atar amma ba wannan ba." Zaune tayi tace "Kana nufin ba zakayi na kenan?" Kai tsaye yace "Eh, haka nake nufi." Cike da gadara tace "Ai kuwa zuwa safiyar gobe mummunan sak'on nan zai sauka idon matarta ka." Yasan barazana ce dan haka yace "And so what? Ki nuna mata mana, kin d'auka mahaukaciya irinki? Wallahi kina nuna mata ba zaki bar gabanta ba har sai kin rasa k'afa ko hannu ko kuma ki rasa fatar jikinki." Jim tayi dan kuwa tasan gaskiya ya fad'a, to ai ita zata fad'awa wani wacece Sameera ba wai wani ya fad'a mata ba, dan haka tayi murmushi tace "Shikenan tunda haka kace, ni kuma zan nuna maka bana maganar banza." Cikin jin haushi yace "Shikenan mu zuba mu gani." Yana fad'a ya kashe wayar, dafe k'ugu yayi ya shiga zarya yana tunanin ta ina ita kuma ta shigo labarin? Ya akayi ta sani ko? Rasa amsa da jin haushi yasa shi buga wayar a bango take ta tarwatse, ganin haka yasa shi fad'awa kan gadon yana dafe da kanshi da hannaye biyu kamar ya kwamtsa ihu da iya k'arfin shi, tabbas yayi bacci amma baisan wane irin bacci bane, domin kuwa abubuwa ne fal a kanshi wanda yasa yake ji kamar ma a zahiri ne idonshi biyu. *Washe gari* Ko da Sameera suka tashi ta d'ora gyaran da suka tsaya jiya, da taimakon su Bilkisu aka had'awa Raihan kayan jikinta musamman kayan bacci wanda ake siyo mata duk jiya, wani abun kam saidai suyi godiyar Allah, ba dan akwai dalar ba antara ta cirewa kawai ake a account da sun d'ora hannu a kai, kasancewar Alhaji Khamis babban mutum ne yace amaryar kawai suke buk'ata, hakan yasa Sameera dan kar a raina mata 'ya ta kashe mata kud'i kamar ba gobe ta fannin sutura wacce zata saka a gani dai, sark'ok'i ma na milyoyin kud'i aka siya mata ga kuma bala'in gyaran da suka saka aka aiko musu daga mai duguri da kuma sokoto, haka ma daga Niger saida aka kawo musu sak'o duk na gyaran jiki a safiyar yau da yake harka da kud'i, misalin *09:00* motoci uku ne suka paka cikin gidan Alhaji Khamis ya turosu su d'auki amarya da masu rakiyarta, sai lokacin kad'ai Abbas ya fito daga d'aki cikin doguwar riga kana ganinshi kaga damuwa, su Ammie da Abba ne da kuma Sameera suka mata nasiha sosai, daga bisani kuma k'annan ta kuka Uka dinga yi na rabuwa da yar uwa wacce aurenta ba zasu shaida komai ba, Raudat taso taje amma haka Abbas ya murje ido yace ai mutum biyu kad'ai zasu rakiyarta, Imranatu da Bilkisu da suka shirya tafiya da kuma Ammie suna ji suna gani sai Bilkisu ta hak'ura su biyu kad'ai, kuka Raihan keyi kamar ranta zai fita , sai duk ta jita kamar wata marar gata, haka suka d'auki hanya bayan hawaye da Sameera ta zubar ita ma. Suna tsaye har suka ga fitarsu, Abbas juyawa yayi ya koma ciki Sameera ma juyawa tayi ta koma d'aki cike da jimamin yar ta, zata zauna kan gado sai kuma ta tsaya tana kallon bak'uwar wayar da bata san da ita ba, d'auka tayi tana k'are mata kallo tana jujjuyata, a saninta dai babu mai ita a mutanen data sani, gashi kuma ba taro akayi ba gidan bare tace wani ya manta, tunanin da tayi ne yasa taja sama sai taga ta bud'e da nufin ko zata samu wata shaida da zata nuna wayar wace, amma bud'awar ita tasa zuciyarta kusan daina aiki yayin da ta nemi numfashinta ta rasa, rawar da k'afafun ta keyi yasa ta durk'ushewa ta saki wayar, banda rawa babu abinda jikinta keyi sai hawayen da suka fara zarya a idonta, idonta sun kafe wuri d'aya kan wayar data fad'i gabanta, tana son d'auke idonta amma abun ya gagara, bud'a baki tayi tana wani irin numfashi da shashek'a duk lokaci d'aya, kai take girgizawa alamar a'a amma kuma ganin abun take yana k'aruwa, wani kukan kura tayi ta mik'e tsaye tare da wayar da gudun tsiya kamar wata yar shekara sha shida ta fita daga d'akin ko kad'an ba zaka rabata da mahaukaciya sabon kamu ba, part d'in shi ta nufa tana zuwa ta kama murfin k'ofar d'akin shi cikin sa'a ta bud'e, tana jin ta bud'e tayi wata fitinanniyar kururuwa tare da cire d'an kwalinta ta shiga d'akin, Abbas da kwantawarshi kenan jin wannan abu yasa shi tashi zaune yana kallon mai shigowa, ganinta a birkice yasan ba lafiya ba dan haka ya yunk'ura da sauri ya mik'e zai tarbeta, ai kamar mai tab'in hankali haka ta... 👏👏👏 26/06/2020 à 19:39 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _23_ Da dare ana ta kai da kawowa na hidimar bikin lieutenant inda aka fara gyara kayan cefanai na girkin gobe sai jiniya da odar motoci kamar zasu fasa unguwar, jim kad'an hayaniya ta fara gauraya gidan sanda mutane ke shigowa, mutanen gidan ne suka fara kimtsawa suna umartar yara da su koma sama, saida mutanen suka fara shigowa falon kad'ai aka fahimci ashe duk dangi ne na wajen Suley da kuma wasu daga cikin dangin Soueiba da mutanen arzik'i, duk girman falon nan sai gashi cike da mutane dan mace tafi talatin wanda suka zo kawo kaya, hakan kuma ya faru ne saboda maganar da Hajia ta fad'awa Husseina shiyasa take so ta bata mamaki. Wata kyakyawar fuskar na gani sak Husseina sai dai wannan tafi d'an tsufa, amma fa ita ma tana cikin shiga ta alfarma da kuma dattako, su Zeinabu da Sa'ada ne suka matsa kusanta suka duk'a suna gaishe ta, cike da fara'a da sakin fuska ta amsa musu kafin ta kallesu a nutse tace "Ina su Ammar ne da Junaid? Yaran nan ko kad'an basa zuwa inda mutane suke sai dai in an zo inda suke." Murmushi Sa'ada tayi tace "Kiyi hak'uri Hajia, kinsan ayyukansu ne sai a hankali." Murmushi tayi ita ma tace "To, haka kuka ce dai, yanzu ina Hajiar take? Kayan jikanyarta muka kawo mata." Zeinabu ce tayi saurin mik'ewa tana fad'in "Suna ciki, bara na musu magana." Sa'ada ce tace "A'a ki barshi, ni zanje." Mik'ewa tayi ta nufi d'akin Hajia, ba jimawa ta fito suka ci gaba da kawowa bak'i ruwa da jus jus wasu ko sanyi babu saboda basu sanar da zuwan nasu ba, minti ashirin Hajia ta d'auka kafin ta fito, fitowarta tasa kowa ya mayar da hankalinshi kan uwar yan uku, masha Allah, shine abinda wasu ke fad'a yayin da wasu ke mamakin rashin tsufan matar, wata arniyar shadda ce tasa yayin da ta watso wasu sark'a da yan kunnai da zobuna da awarwaro na zinariya, ba dan komai ba sai dan ta bayar da tsoro, dan hayaniyar da taji tasan ba zasu yarda su mata wannan gayyar ba babu wani dalili, wani d'aurin d'an kwali ne ta kashe mai sauk'in gaske wanda yasa manyan kitsonta sauka har gadon bayanta, kwalli ne kad'ai a idonta amma tayi kyau sosai sai d'aukar ido take ga jar fatar nan tayi wani shek'i, kamar d'awisu haka ta tako har ta zo kujerarta ta zauna tana shan k'amshi da k'arewa mutanen kallon hadarin kaji kallon mai bisa ruwa. Wannan Izzar ta ta da kwarjini yasa wasu daga cikin matan ma suka manta da matsayinsu suka fara gaisheta, tabbas suna jin muryarta na amsawa amma basu ganin labb'anta na motsawa, nan dai *Hassana* (yar uwar Husseina) ta umarci a shigo da kayan, mace uku ce ta mik'e suka d'auko akwatinan masu bakwai bakwai a ciki har kala uku, da kuma d'aurin goro har guda biyu, har gaban Hajia suka diresu tana kallon akwatinan, wani matashin saurayi ne ya shigo da wani dallelen moton har falon ya aje shi inda babu mutane a ledarshi, Hassana ce ta kalli Hajia tace "To alhamdulillah, kayan Jibril ne muka kawo na Jamila, ga akwatina, ga moton da yace a kawowa amaryarsa dan ci gaba da zuwa makaranta, sai kuma..." Ta fad'a tana saka hannu cikin jakarta ta fito da kud'i ta d'ora saman d'aya daga cikin akwatinan tace "Sai wannan, million biyu ne, sadakinta kuma sai ranar d'aurin aure." Ko ba komai bajintar tasu ta birge Hajia, amma saita dake ta kalli Hassana wacce ita ma ba shiri suke ba tace "Ba laifi, amma yasan da cewa buzuwa zai aura ta b'angare na, ba zai birge ni ba har sai yayiduk wani abinda akeyi idan za'a auri buzuwa." Wani murmushin gefen labb'a Hassana tayi tace "Wannan ba matsala bane, sai dai zaifi kyau ki fad'a mana yanda al'adun suke dan mu sani, duk da shima dai akwai abinda dole amaryar tayi kasancewarshi babarbare." Wata hamshak'iyar dariya Hajia ta saki wacce ni dai tunda na fara rubutun nan banji inda tayi dariya ba, kallon Hassana tayi tace "Babarbare? Ta ina? B'angaren uwa?" Murmushi tayi kafin ta kawar da kanta tace "Ba zan tsawwala muku ba, ina so kawai naga anyi guitar (jita) a daren d'aurin aurensu, za ayi shiga irinta buzaye ko kuwa mutum baya so, sannan ba wai Jibril ba kad'ai, har sauran angayen dole kowane ya kawo min kyautar rak'umi wanda ya amsa sunan rak'umi bayan tarewarsu da matansu, hakan kuwa shine zai sake nuna darajar yaran da kuma d'aga martabarsu." Wani kallo Husseina dake gefe ta mata tace "Amma ai na d'auka wannan al'adar ana cikata ne idan aka samu yarinyar da mutuncinta?" Murmushi Hajia tayi ta kalleta tace "Kina tsammanin duk yanda nake saka ido kan 'ya'ya da jikokina za'a iya samunsu da rashin kamun kai, ai wannan ba abu bane da za'a same shi a zuri'ata ba." Murmushi Husseina tayi ta sassauta muryarta tace "Ke ina taki kyautar?" Hassana ce ta kalleta sannan ta kalli Hajia tace "Ba damuwa, zamuyi duk abinda kika ce, ai Jamila da Jibril yan uwan juna ne, ko kyauta zai iya siya mata jajayen rak'uma bare kuma ya karb'i budurcinta." Suna kammalawa sukayi sallama inda Hajia ta bud'a jakar hannunta k'arama ta bawa Sa'ada kud'i har jaka d'ari biyu tace ta basu tukuici kamar yanda akeyi, su kansu k'in amsar tukuicin sukayi suka ce ai yayi yawa, da k'yar Sa'ada ta matsa musu suka karb'a suka bar gidan kowa da abun fad'a a baki. Suna tafiya Ummy ta zarce b'angaren samarin ta shiga da sallama, Amar Jibril da Junaid da kuma Ammar ta samu zaune a falon, gaishe ta sukayi dukansu banda Ammar da hankalinshi ke kan tv, zaune tayi tana kallon Jibril tace "Bak'i har sun tafi, munga kaya masha Allah, Allah ya sanya alkairi?" Da murmushi ya amsa da "Ameen aunty." Kallon Amar tayi tace "Saura ku, na ku sai yaushe?" Amar ne yace "Ummy gobe mu ma zamu kawo." Dukansu ta kalla tace "Sai kun shirya da kyau, dan Hajia tace za'a gudanar da wasu daga cikin al'adunsu na buzaye, musamman ma ku." Ta fada da nuna su Ammar ta ci gaba da cewa "Tunda kunga ni kaina buzuwa ce, dan haka dole zata fi karkata abun ta b'angaren ku." Amar ne yace "Ba damuwa bane Ummy, matsalar ni dai wannan k'aton rawanin ne bana tunanin zan iya d'aurawa." Dariya tayi tace "Da kaina zan d'aura maka, tunda saika d'aura shine zaka fito a buzun." Mik'ewa tayi tace "Saida safenku, ku kwanta da wuri kunsan gobe ne fa auren ubanku." Sai lokacin Ammar ya kalleta ta wutsiyar ido ya kuma d'auke kan shi, fita tayi inda Ammar ya mik'e zai shiga d'aki, Amar ne yace "Ka tabbatar ka tashi da wuri fa, dan Abba yace ni da kai ne zamu take masa baya muna karb'ar bak'i." Juyowa yayi ya kalleshi k'ala baice ba ya shige ciki ya barsu, Jibril ne ya gyara zama yace "Yau fa mutanen sun motsa." Murmushi Amar yayi yace "Allah dai ya kyauta." "Ameen." Cewar Junaid. A nesa da k'ofar gidan ya paka mota ya tsaya inda kawu Mamu ya shiga dan kiran Zeituna, ba laifi gidan ya kaure da cacaniya alamar dai biki za ayi gobe, tuni dama ansa Zeituna ta shirya cikin wani kalar d'inki na atamfa wanda ba dan ta sanya hijab ba sai a mata dariya, dan kaf dangin babu mai wayewa ta zamani haka ita ma, dan ba k'awaye gareta ba bare tasan abu mai kyau ko marar kyau, lalle da kitso ma tayi sa'a a unguwar aka samu wanda suka iya suka mata, wata doguwar jagira aka ja mata tare da shafa mata jan jan-baki, fitowa tayi tana hard'e k'afafu saboda tsoron abinda zata tarar, tana isa ta inda yake ta tsaya kanta k'asa, tunda ta taho lieutenant ke hangenta yana raya abubuwa da dama, tana tsayawa ya sauke gilashin murya a d'an kausashe yace "Sai ki shigo ko, kinga ni ba yaro bane bare na fito na tsaya kowa na kallo na." Gabanta ne ya tsananta fad'uwa ta zagaya ta kama k'ofar ta shiga, da k'yar ta janyo k'ofar ta rufe ta sake mayar da kanta k'asa tana wasa da yatsunta daga cikin hijabi, kamar yace ke ta zuba a guje take ji, wai yau gata a mota da Abban Ammar ana shirin d'aura musu aure gobe, jin shirun ne yasa ta tsargu ba tare data d'ago ba tace "Ina wuni." Ajiyar zuciya ya sauke dan dama yana jiran tayi magana ne, kallonta yayi yace "Lafiya lau, ya hidima?" Shiru tayi kamar ba taji ba, kallonta yayi kamar ya shareta sai kuma yace "Tun yaushe kike so na? Kuma kina ganin hukuncin da Alhaji ya yanke bai tauyeki ba? Har zuciyarki zaki iya zama da ni?" Zeituna dake jin tambayoyinshi kamar saukar guduma a kanta tasan ba zata iya amsawa ba, sai kawai ta fashe da kuka tasa hannu ta toshe baki, sororo yayi yana kallonta da mamakin kukan na meye? Wani abu ya fad'a daya b'ata mata rai? Ko kuma sangarta ce tana so ya fara rawar k'afa yana rarrashinta? Ai ko abinda ba zai yiwu ba kenan, fuska ba annuri yace "Meye na kuka kuma? Na fad'i wani abu ne? Ko kuma dai takuraki akayi?" Girgiza kai tayi hakan yasa yace "Shin akwai wani abu da kike buk'ata ne?" Nan ma girgiza kai tayi hakan yasa ya kawar da kansa yace "To ni zan tafi, saida safe ko?" Ji tayi wani kukan ya taho mata wanda yasa tayi saurin bud'e k'ofar ta fito, rufewa tayi ta taka da hanzari ta tunkarin gidan, saida ya ga shigarta kad'ai ya ja d'an k'aramin tsaki ya tayar da motar ya bar unguwar. *11: 49* na dare Ammar ya mik'e zaune tsakiyar gadonshi, tsaki yayi tare da kama hantsar wandonshi yace "Shikenan mutum idan baida aure baya da nutsuwa har abada." Sakin wandon yayi ya sauko daga kan gadon, ban d'aki ya shiga ba wani jimawa ya fito, rigar wandon baccinshi ya d'auka fara ya saka ya fito, duk wani kwanon abinci daya gani a falon nasu saida ya duba amma babu abinci, fridge ya duba nan ma sai lemu kawai da ruwa, wani tsakin ya kuma ja tare da nufa k'ofar fita, acan bayan gida yake jin hayaniyar matan suna aiki, kai tsaye falon Hajia ya shiga wanda ke bud'e har yanzu saboda matan basu shiga ba bare a rufe, madafa ya wuce da niyyar shiga sai yaji k'ofar a rufe, baiyi mamaki ba dan dama idan dare yayi ana rufe k'ofofin ko ina, dawowa yayi da niyyar fita kawai dan ba zai iya jura jin bak'ar magana daga bakin kowa ba, ta kusurwar d'akin Alhaji yabi zai wuce sai yaji motsi, d'an murmushi yayi ya matso ya kama k'ofar zai bud'e sai yaji muryar Alhaji na magana da alama addu'a yake yana fad'in " *Allah kaine Allah, Allah kai kace mu rok'eka zaka amsa mana, gashi ina rok'onka kaina k'asa, Allah ka kare min zuri'ata da ahalina, Allah ka karesu daga aikata alfasha, Allah ka kare min 'ya'ya da jikokina daga sharrin zina, Allah ka kub'utar dasu da ikonka, Allah kai shaidane ban tab'a aikata zina ba, ban tab'a k'etara iyakar wani ba ta hanyar cin zarafin iyalinshi, amma ya zama dole na rok'awa iyalina kariya saboda sharrin zamani, sannan iyali suna kimtsuwa ne idan ka zab'ar musu uwa ta gari, nayi kuskure tun farko dana amince da auren Zeeya'atu, duk da a waccen lokacin ina da k'arancin ilimin addini ban kuma farga ba saida muka hayayyafa, Allah ina rok'onka ka kare min zuri'ata kada zunubin zina da mahaifiya ko kakarsu ta aikata a lokacin k'uruciyarta ya shafesu, Allah ka nesanta su da laifin zubar da cikin da mahaifiya kuma kakarsu tayi kar ma ya shafesu daidai da k'wayar zarra, Allah ka sani baiwar nan taka har yanzu bata neman shiriya daga waccen laifin, kullum tsanar mazinata take k'arawa a zuciyarta saboda tasan muninta, Allah ka shiryeta dan tsarkin mulkinka, Allah ka farkar da ita ta gane kurenta na baya ta buba gareshi, astagfirullah, astagfirullah, astagfirullah ya Allah.*" Jin wannan addua'r yasa Ammar sakin k'ofar yayi jim, Hajia? Hajia dai, wannan shine dalilinta na tsaurara sa idonta akan zuri'ar ta kenan? Wannan shine dalilin da yasa take k'in yayan da aka haifa bata hanyar aure ba? Ashe ita ma tayi rayuwarta a baya ta holewa? Kukan da cikinshi yayi ne na yunwa ya farkar da shi daga tunaninshi, dafe cikin yayi ya juya ya kalli d'akin Ummy, murtuke fuska yayi kafin ya tukari d'akin da niyyar tambayarta makullin madafa, dan ba zai tambayeta abinci ba yasan zata fad'i bak'a ne, yana isa ya zura hannu zai bud'a sai yaga k'ofar ba rufe take ruf ba, turawa yayi ya ga ta bud'e sai kawai ya shiga cikin takon isa da k'asaita. Mahaukacin turarenshi ne ( *Respond*)ya ganar da ita shine, da sauri ta d'ago ta sauke ido a kanshi saida gabanta ya fad'i, mamaki take meya shigo dashi a wannan lokacin d'akin Ummy? Dare fa yayi, shi kanshi mamaki yake ganinta a tsakiyar gadon Ummy zaune da littafinta na makaranta da kuma farantin kankana a gabanta, cikin kallon tuhuma ya tsaya gaban gadon fuska a had'e yace "Me kike anan d'akin?" D'auke idonta tayi daga kanshi ta harareshi ta wutsiyar ido a zuciyarta tace "Kai baka ga abinda nake bane?" A zahiri kuma cewa tayi "Karatu nake." Cike da kallon raini yace "Yawon biki ya hanaki d'aukar darasinki ko? Da alama kuma jarabawa zakuyi gobe, to Allah yasa ki fad'i watak'ila ki shiga hankalinki." Baki bud'e ta kalleshi da mamaki irin wace irin magana ce wannan? Fahimtar kallon yasa shi cewa "Eh naje na fad'a, ko zaki ci min uwa ne?" Wani murmushin baka da hankali ta masa tace "Ah haba dai ranka shi dad'e, ni na isa, Allah dai ya k'ara girma." "Zaki iya mana, ba kece sarauniyar ce min Allah ya isa ba." Yanda yayi maganar yasa ta zabura ta durka daga kan gadon da nufin shigewa ban d'aki, da sauri yasha gabanta ya tsaya k'ik'am, sai lokacin ya k'are mata kallo ya fahimci ashe wando ne iya gwiwa a jikinta da rigarshi saidai basu kamata ba, sai wata hula data saka bak'a mai duwatsu masu k'yali a gabanta, kasancewar yafi ta tsayi sosai yasa yayi k'asa da kanshi yana kallon k'irjin ta wanda da gani kasan rigarce kawai babu bras, kawar da kanshi yayi ya d'an cije leb'e, ba tare daya kalleta ba yace "Koma ki zauna, ai idan na tashi hukuntaki duk inda zaki shiga zan biki." Turo baki tayi gaba ta kalleshi kamar zatayi kuka, yana kallonta yayi saurin d'auke kanshi ya furta "Ya Allah." Lumshe ido yayi ya d'aga kai sama, wannan yanayin da tayi ba k'aramin tashin hankalinshi tayi ba, "Meyasa take birgeshi wani lokacin?" Kafin ya samu amsa ya sake kallonta rai a b'ace saboda halin da take k'ok'arin jefashi yace "Ki koma ki zauna na ce." Kamar sakara haka ta saki baki da tunanin to meyasa kai ba zaka tafiyarka ba? Juyawar da tayi ita tafi sa shi yin nadama, gaskiya Allah ya musu hallita ta wannan fanni kam sai godiyar Allah, juyawa yayi ya zagaya inda ya fara tsayawa ita ma ta koma ta zauna, kankanar da take sha ya d'auki yanka d'aya yasa a baki ya guntsira, wani matashin murmushi yayi yace "Kankana." Kallonshi tayi sai kuma ta mayar da kallonta ga littafinta, sauran daya rage hannunshi ya mik'o mata da fad'in "Sha." Wani yamutsa fuska tayi alamar k'yama k'arara, sake zuro mata yayi kamar zai saka mata a baki hakan yasa tayi saurin kawar da kanta, cikin tsawa yace "Karb'i nace." Juyowa tayi tasa hannu ta karb'a zata aje yace "Cewa nayi kisha." Kallon fuskarshi tayi tana d'an nuna mishi da hannu cike da k'yama tace "To ai yah Ammar ni...wallahi bana son wannan..abun ne." Kafeta yayi da ido yace "Meye ba kya so?" Saida ta matsa baya kafin tace "Ka gane yah Ammar, gaskiya ba zan iya sha ba saboda wannan dogon gashin na fuskarka." Na farko daya kalleta da mamaki, wai dogon gashin fuskarshi, tana nufin gemunshi fa? Gashin da man da yake shafa mishi ma wata rana saiya zagaye garin nan bai samu ba sai yasa abokanshi da sukayi karatu a France sun aiko mishi, shine za tace wai tana k'yama, shi kam ya zaiyi da kankana ne? Kama gemun yayi yana shafawa tare da kallonta, can ya saki wani murmushi na mugunta, ba tare daya daina murmushin ba yace "Wato kina k'yamarshi ko?" D'agowa tayi ta kalleshi, ganin kallon da yake mata yasa ta sauka daga kan gadon da gudu ta nufi ban d'aki, harta kama hannun k'ofar taji yayi ram da k'ugunta ya dawo da ita baya, mannata yayi jikin bango ya mata runfa da gaba d'aya jikinshi. Tunda yake ritsata bai tab'a mata irin haka ba, hakan yasa ta tsorata sosai jikinta ya fara b'ari ta fara inda inda, cikin rawar murya tace "Dan Allah yah Ammar ka matsa, hakan fa bai dace ba." Sunkuyo da kanshi yayi yasa dogon gashin da bata so yana mata yawo dashi a wuya har zuwa fuskarta yana shafa mata shi, tattausan k'amshin turarenta ne ( *Feminism*) yayi tasiri sosai wajen sa shi ya sake fita hayyacinshi, rufe ido tayi tana kawar da kanta tana jin tsikar jikinta na tashi wani bak'on yanayi na shigarta, yatsanshi yasa ya tallabo hab'arta, k'urawa fuskarta ido yayi yanda ta rintse ido tana kakkaucewa, cikin wata irin murya yace "Wato wannan ne baki so ko?" Jin yana ci gaba da shafar fuskarta da gashin yasa tasa k'arfi ta tura shi baya tana fad'in "Dallah ni ka matsa min, wannan wane irin iskanci ne? Bana son irin wannan wasar fa." Ko motsi baiyi ba bare tasa ran zai gusa daga kanta, matse damatsanta yayi sosai ya jijjigata yana fad'in "Ke kina iya tunanin matsawa daga nan ne? Ai tunda kika nuna kina k'yamar gashi na ta yanda ba zan iya shan abu kisha ba, to kuwa dole yawu na da naki su gauraya." Wuyanta ya cabko ta baya ya d'ago kanta ya daidaita bakinta ya kai nashi bakin, tana jin bakinshi a nata tasa k'arfi ta fara tureshi, amma gam ya sake lik'e mata saboda jin dad'in abinda yake yi da mantawa a ina yake me kuma yake yi. _Dan Allah duk wanda zai karanta page d'in nan ya fad'i alkairi ko yayi shiru, karku manta da cewa abune daya faru a zahiri, addu'a da fatan shiriya ita wasu mutanen ke buk'ata, kar mu manta da Hajia wace irin mace ce da kuma mummunar kalmar da kullum iyayenshi ke binshi da ita, musamman kalmar *d'an iska* da *shege*, so mi bishi da addu'a kawai dan dole wata rana dama addua'r tayi tasiri a kanshi, tunda shi ba zai iya zama shege ba sun mishi gatan samar dashi ta hanyar aure, to fa dole suyi hak'uri dan zasu goyi jikan shege, Allah kasa mu dace._ Sosai yake tsotsar bakinta ya manta da ba halak d'in shi bace, ita kuma kokawa take dashi sosai duk da ya rik'e mata hannayenta sosai, zura hannayenshi yayi cikin rigarta sai kawai yayi karo da tula tulan... Jinsu a tafin hannunshi yasa ya saki bakinta ya zuro d'aya daga cikin na shanunta ta saman rigar ya kai bakinshi yayin da d'aya hannun ya rufe mata baki dashi, a lokaci d'aya kuma yake tahowa da ita har yayi nasarar kwantar da ita ka gadon, kuwa take iya k'arfin da tunanin a kawo mata d'auki tare da kokawa iya k'arfin ta tana dukanshi tana cizon tafin hannunshi daya rufe mata baki... 👏👏👏 19/07/2020 à 19:25 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _24_ Aikin gama kam ya gama, rana ta farko daya fara sanin 'ya mace a duniya kamar yanda ita ma shine na farko gareta, zaune yake bakin gadon yana bubbuga kanshi da hannayenshi yana so ya farka daga mummunan baccin da yake, amma ganin ya k'i tashi yasa ya mik'e da k'arfi tare da kaiwa bango naushi yana fad'in "Meyasa? Meya sameka Ammar? Me ka aikata? Tirr da kai." Fuskantar gadon yayi idonshi rintse baya son ganin Hamna a wannan halin, saida ya sauke numfashi mai k'arfi kafin ya bud'e ido a hankali da addua'r Allah yasa yagababu kowa kawai gizo ne ko mafarki, tarau ya sauke ido kanta tana jan numfashinta da k'yar sai matsawa take har tana neman fad'uwa daga kan gadon tana kuka, kallonshi ya kai kan ta'asar da yayi hakan yasa shi cabko wuyanshi ta baya da k'arfi ya sake rintse ido yace "Shiiit, Ammar alawadaranka, ashe dama d'an iska ne kai kamar yanda suke fad'a, meya kaika aikata wannan b'arnar?" Hamna data sauka daga kan gadon ne ta rakub'e ta had'a kai da gwiwa tana ta k'ara dunk'ulewa cikin zanin gadon data janyo ta rufe jikinta sai k'ara sautin kukanta take, lallai yau ta koyi wasu darusa da dama na rayuwa, na farko ta fara jin *tsoronshi* ta yanda take jin ba zata sake shiga harkarshi ba, na biyu kuma ta *ji wata tsanarshi ta gauraya jini da tsokarta*, na uku kuma duk *abinda Allah ya hukunta* shine zai sameka ko baka so, domin kuwa saida Ummy tace mata ta rufe d'akin saboda ko bacci ya d'auketa tunda su suna aiki basu ga ranar gamawa ba, sannan har yer uwarta Amna saida tace me zaisa taje d'akin Ummy karatu bayan ga nasu d'akin, bata tunanin Abba ya dawo ya kuma buk'aci d'akin? Amma haka ta shareta ta taho, ashe wannan mummunar k'addarar ce ke bibiyarta, bak'ar ranar da d'an uwanta na jini zai mata fyad'e, ita kam tsakaninta dashi sai Allah isar mata, dan kuwa ba zata yafe masa ba har abada. Kallonta yayi duk yanayin tashin hankali da rashin jin dad'i ya bayyana a tare dashi, kallon littafinta yayi na karatun wanda ya turmushe da kuma kankanar data zube, girgiza kanshi yayi yana tunanin ta ina ma zai fara rarrashinta? Da wane ido zai kalleta yace zai bata hak'uri? Me zai fad'a mata ta yarda dashi? Wane kallo mutanen gidan nan zasu mishi? Ya ma akayi ya zarce daga ya d'an mata horon da bai wuce sumbata ba? Sai kawai ya tsinci kanshi yana sukuwa akan 'yar mutane yana hak'arta kamar rijiya, bayan kuma babu aure tsakaninsu, kai Ammar ya ma zakayi da yer uwarta ne wacce kayi niyyar aura? Me zata ji? Yer uwarta da suka fito ciki d'aya? Rashin samun madafa ya sashi sake kaiwa bango dukan tsiya wanda yasa har saida jini ya shake gabce mishi sanadiyar ciwon da yaji ranar, da saurin bala'i ya bud'e k'ofar d'akin ya fita dan hakan shine ma daidai a wurinshi, saida ya zo zai wuce ya kalli k'ofar Alhaji, ji yayi wasu hawaye na neman taho mishi na tausayin tsohon, mintuna nawa ne daya saurari addua'r shi, amma ace haka ta faru dashi, lallai wannan k'addara ce, dan ba dan Allah ya rubuta hakan zai faru ba da babu abinda zai fito dashi neman abincin ci, duba da yasha kwana da yunwa kuma baya damuwa, sannan ko da *11:00* na dare Hajia tasa an rufe mata k'ofar falon nan, amma yau sakamakon sabga yasa ba'a rufe ba har ya iya shigowa, sannan da farko yayi niyyar barin d'akin, amma addua'r Alhaji data tsayar dashi har tasa yaje d'akin Ummy, gashi yanzu ya aikata abinda baisan ina tashin hankalin zai tsaya ba, da sassarfa ya taka zai fita ba tare daya lura ba yayi karo da mutum, da sauri ya kalli wanda suka had'u ashe Ummy ce rik'e da jug na ruwa, wani kallo ta masa kamar zata cinyeshi tace "Kai kuma meye haka? Me kake yi anan a wannan lokacin?" Kafeta yayi da ido kawai dan rashin gaskiya yasa yana tunanin kamar zata karanta a goshinshi abinda ya faru, shirun daya mata yasa taja dogon tsaki ta wuce ta barshi nan, da sauri shima ya fita ya koma b'angaren su ko k'ofar bai rufe ba ya wuce d'akin shi, yana shiga wanka ya shiga yayi na tsarki kafin ya tsaya gaban panpo yana sako mishi ruwa, ido rufe ruwan ke sauka yana hasko duk abinda ya wakana, "Tabbas nine na fara bud'e kankana, ni ta fara sani, ashe duk wayewar nan tata bata sa ta zubar da mutumcinta ba, ina ma ta hanyar aure hakan ta faru?" *Ummy* na shiga d'akin ta tsaya turus saboda ganin bak'in abubuwa, babu zanin gado shinfid'e sai ma alamun jini-jini, farantin kankana tarwatse tare da kankanar, littafin karatu ya turmushe sai kuma pilow dake kan gadon suma duk a k'asa, tana cikin duba wannan abubuwan ne taji sautin kukan Hamna, saida ta sake kallon wurin da kyau tare da matsowa kad'ai ta ganta, ganin dunk'ule cikin zanin yasa Ummy sakin jug d'in ta k'arasa da gudu ta durk'ushe ta rik'ota tana fad'in "Subhanallahi, Hamna lafiya? Meya sameki haka? Meya faru dake? Lafiya k'alau na barki, meya faru?" Hamna sake fad'awa tayi jikin Ummy ta sake fashewa da kuka sosai, gaban Ummy ne ya ninka fad'uwa tare da k'arfin halin cewa "Hamna dan Allah ki fad'a min, meya faru na ganki?" Kuka kawai take ta kasa cewa komai tana tunanin ta fad'a ko tayi shiru, Ummy kuma data gama fahimtar meya faru hawaye ne suka taho mata ta k'ara k'amk'ame Hamna a k'irjinta tana fad'in "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Hamna Ammar ne?" Kukan data sake fashewa da shi ne yasa Ummy ma fashewa da kukan da k'arfi, d'ora bakinta tayi kan gashin Hamna har hawayenta na zuba saman kan tana fad'in "Hamna kiyi hak'uri, laifi na ne, laifina ne Hamna, kiyi hak'uri dan Allah, Ammar ya zamar min kamar dodo, bansan me nayi masa ba da yake son ganin ya d'ora min hawan jini, ba zan tsine masa bane kawai dan kar ya k'arasa zamar min tashin hankali." Kuka suka ci gaba da rerawa kafin daga bisani Ummy ta d'agota ta kalleta ta dafa kumatunta tace "Hamna kiyi hak'uri kiyi shiru kinji, bara na taimaka miki." Mik'ewa tayi ta shiga ban d'aki, heater ta kunna mata ruwa masu yawa kafin ta fito ta fara gyara d'akin, duk tana aikin nan tana zubar da hawaye na takaicin abinda Ammar yayi, tana tunanin abinda zai faru idan mutan gidan nan suka samu labari, da wane ido zata kalli mahaifinshi? Me zata fad'awa mahaifiyar Hamna da mahaifinta ma? Wane irin kallo zasu mata? Me zasu ce? Hajia fa? Babban tashin hankalin kenan Hajia? Da wannan tunanin ta gama kimtsa d'akin taje tasa ma k'ofar d'akin makulli ta rufe sannan ta kamata suka shiga ban d'aki, saida ta nuna mata ta shiga cikin bahon wankan suka lura da jinin dake bin k'afafun ta, a marairaice Ummy ta kalleta tace "Ki shiga kiyi wankan, idan kika fito saina dubaki watak'ila kinyi k'ari ne." Shiga tayi ita kuma ta fito ta d'auke zanin gadon da tattare kayan jikinta, duk da basu yage ba amma sunji matsa, ta jima tana jiran fitowarta kafin ta fito ta zaunar da ita, wani zama tayi kamar akan wuta saboda zafin da take ji zaman ma tayi ne dan Ummy ce ta zaunar da ita, kallon kumburarrin idonta Ummy tayi ta dafa kafad'ar ta tace "Hamna zan iya rok'onki wata alfarma? Dan Allah? " Cikin lumshe ido ta kalleta tana cije leb'en k'asa ta jinjina mata kai kawai alamar eh, nisawa tayi tare da kallonta a tsanake tace "Hamna, bansan taya zan fara baki hak'uri akan abinda ya faru ba? Haka bansan meya had'a ku ba har haka ta faru? Amma dai Hamna aikin gama ya riga daya gama, muyi tunanin abinda zai biyo baya Hamna idan abu nan ya fito fili, Hamna, shin kina son zumuncin dake tsakanin mahaifinki da mahaifinshi ya wargaje? Ko kuma zaki so mutumcin dake tsakani na da mahaifiyarku ya tarwatse? Ko kuma zaki so ganin Hajia cikin wani mawuyacin hali sakamakon abinda ya faru dake?" Hamna da duk ta fahimci inda kalaman Ummy zasu dosa ne cikin muryarta data disashe tace "Ummy na fahimci me kike nufi, ba sai kin rok'e ni kan nayi shiru ba, nima abinda nake tunanin rok'onki kenan, Ummy ba zan so kowa yasan abinda ya faru dani ba, ba lallai zumuncin iyayenmu ya tab'u ba saboda duka iyayena suna k'aunar shi, amma ni zan ji kunyarsu, sannan bana so Hajia ta sani dan zata tsine min tare da shi, sannan Ummy..." Fashewa tayi da kukan hakan yasa Ummy k'ura mata ido tana kallo, da k'yar ta tsagaita ta ci gaba da cewa "Ummy yer uwata Amna, ita ce fa wacce zai aura, kuma kinsan Hajia ba canza maganarta take ba, Ummy da wane ido zan kalleta idan tasan...idan tasan mijin da zata aure ne ya min..." Hannunta Ummy ta kamo tace " 'Yata hakan yana nufin wannan ya zama sirri a tsakaninmu kenan?" Jinjina kai tayi cikin kuka alamar eh, rumgumeta Ummy tayi tana fad'in "Nagode Hamna da kika fahimce ni, nagode da kika yarda zaki rufa masa asiri, tabbas ni uwa ce, amma karki d'auki hakan a matsayin tauye miki hakk'i, nasan an zalinceki sosai ta yanda ba zamu iya dawo miki da abinda ya fizge miki ba, amma lokaci zai zo da zaki gane hakan da nayi shine gatan daya dace na miki." D'agota tayi tace "Ki kwanta na dubaki na gani." Kunya ce tasa tace "Ba komai Ummy ki barshi kawai." Kwantar da ita tayi tace "A'a ba zan yarda ba Hamna, tun yanzu ne ta kamata na dubaki dan nasan waccen d'an banzan ba hankali ne dashi ba, kaca-kaca ya miki da gani ma." Sunkuyar da kai tayi wasu hawaye suka zuba kan k'afafun ta, tana ji tana gani Ummy ta bud'eta ta dubata, kuma tabbas akwai k'ari wanda inba d'inki aka mata ba zai iya haifar mata da matsala a gaba, cike da tausayi Ummy ta kalleta tace "Hamna kin k'aru fa sosai, gashi dare yayi yanzun nasan duk inda kawunku yake yana kan hanyar shigowa gidan, dan nasan wannan hidimar ce ta hanashi shigowa da wuri, ya kamata na miki d'inki, bansan ko zaki iya jurewa ba yanzun?" Cikin zubo da wasu hawayen taysayin kanta tace "Ummy tsoro nake ji gaskiya, kawai ki barshi ma ba komai." Cike da gargad'i tace "Hamna akwai komai, ba zaki fahimci haka ba sai kinyi aure ko kuma kin haihu, gaskiya ba zan iya kallonki haka ba." Wani kallo ta ma Ummy, sai tayi aure? Kai amma boss ya cuceta, yanzu shikenan fa ya rabata da mutumcinta ta k'arfi? Kuma ya auri yer uwarta ita ma ya moreta, riba biyu kenan, ya jini ya ji yer uwata, k'wank'wasa d'akin Ummy akayi tayi sauri ta dauk'owa Hamna littafinta ta bata a hannu tace "Ki saki fuskarki dan Allah kar wani ya fahimta." Mayar da kanta tayi ga littafin ta yanda ma mai shigowa ba zai iya ganin fuskarta ba saita juya ko kuma shi ya shigo har inda take, Ummy na bud'ewa Jamila da ake aiki tare dasu ne tace "Aunty wai ki zo inji Mama." Murmushi tayi mata tace "Shikenan kice ina zuwa." Murmushi tayi ita ma tana kallon bayan Hamna tace "Yan biyun Ummy wacece a cikin? Ku ba zaku fito muyi aiki ba?" Murmushin yak'e Ummy tayi ta juya ta kalli Hamna da ko juyowa ba tayi ba tace "Hamna ce, karatu take saboda jarabawarsu gobe." Juyawa tayi ta fita Ummy kuma ta juyo ta kalleta tace "Hamna zan tafi naji, dan Allah ki saki ranki kinji, komai dare idan na dawo zan miki d'inkin nan." Da kallo kawai ta bita harta fita, juyowa ta sake yi a hankali ta zubawa littafin ido, Ammar ne ya sake dawo mata a tunaninta tun daga shigowarshi har abinda ya faru, fita yayi ma ko bata hak'uri bare ya rarrasheta, a hankali ta furta "Allah ya isa, mugu kawai azzalumi mai bak'ar zuciya, wallahi sai mun tsaya gaban Allah ya mana hisabi." Ummy na zuwa naman da aka soya ne Zeinabu ta tambaye ta yanda zasuyi dashi a matsayinta na babba garesu, tana fad'a musu yanda zasuyi tace tana zuwa ta bar wurin, b'angaren su Ammar ta nufa a harzuk'e tayi sa'ar shiga saboda k'ofar a sake, tana zuwa k'ofar d'akin shi ta bud'a da k'arfi ta shiga, zunbur ya tashi tsaye dama zaune yake bakin gadon da towel ya fito daga wanka ya kasa katab'us, yana ganin Ummy ce kuma yanayin fuskarta ya nuna mishi abinda zai faru, shi kuma yau ya yarda yayi laifi kuma zai bayar da hak'uri, dan haka kafin ta k'araso ya durk'usar da gwiwoyinshi k'asa ya sanda kanshi yana jiran hukunci, Ummy na zuwa gabanshi ta d'auke shi da mari har saida ya tangad'a, yana dawowa daidai ta sauke kai mishi wani marin a d'aya kumatun tasa k'afa ta hankad'ashi ya fad'i warwas k'asa, tashi ya sakeyi ya koma yanda yake a farko yana kallonta yace "Ummy ki min duk hukuncin daya dace dani, wallahi zan d'auka, amma dan Allah karki tsine min Ummy, ba zan iya jurar tsinuwarki ba, Ummy kada ki zageni dan Allah, dan bansan inda hakan zai sake kaini ba." Cikin zafin rai ta sake kashe shi da mari duk da rad'ad'in da hannayenta keyi, sunkuyawa tayi kamar zata fad'a kanshi ta nuna kanta tace "Ammar me nayi maka? Me na aikata maka da wannan hukuncin ne kad'ai ya dace dani? In haifeka a ciki na amma kullum burinka shine kaga ina zubar da hawaye, akan me Ammar? Meya kaika d'aki na a daren nan? Me tayi maka da sai kayi mata fyad'e ne kad'ai zaka huce? Ammar akan wane dalili ne kake son raba zumuncin dake tsakanin iyayenku? Kasan abinda hakan zai iya haifarwa kuwa? Baka sani ba? Kawai kenan iskancinka ne ya motsa ka kuma rasa inda zaka sauke shi sai akan yer uwarka, yarinyar daka rainesu a hannayenka, yarinyar da kake nuna baka k'aunar ta, babu abinda ka saba mata dashi sai muguntarka, yanzu shikenan ka ida zama dodo a wurinta, kasan irin b'arnar da kayi? Ka lalata mata komai, ka k'wace abu mai daraja a gurinta, tirr da hali irin naka, wai kai kana da zuciya ma a k'irjin ka? Meyasa da bak'ar jarabar taka ta taso baka fita ka nemi matan banzan daka saba bi ba, dan ba zan tab'a yarda da kai ba idan kace min baka tab'a yi ba sai yau, dan ta'asar da kayi tafi k'arfi ta d'an koyo, alamu ne na wanda ya saba kuma a dole yake neman sauk'in jarabarshi." K'ura masa ido tayi tana kallo hakan yasa shi kama k'afafun shi cikin kukan jin zafin kalamanta yace "Ummy ki yarda dani, wallahi ni ba d'an iska bane, ban tab'a zina ba, dan Allah Ummy kiyi hakkk..." Bai k'arasa ba ta fizge k'afafun ta ta juya zata bar d'akin, tsayawa tayi bakin k'ofar ta juyo ta kalleshi tace "Ammar ka tabbatar min kai tantagaryar d'an iska ne na gidan gaba, nagode maka." Da sauri ya d'aga kai ya kalleta da tsantsar mamakin jin furucin daya fito daga bakinta tare da jin zafi a zuciyarshi, jinjina kai tayi tace "Eh, saboda kai iskancin naka daya tashi ma a cikin gidanku kayi, a cikin gidanku ma akan k'anwarka, da k'anwar taka ma kuma Ammar cikin d'akina, d'akin mahaifiyarka, akan gadon iyayenka, Ammar wace irin lalacewa ce wannan? Ka kwanta da yarinya akan gadon da iyayenka ke kwanciya, Ammar abinda ya faru ya isa yasa na tsine maka albarka ka shiga duniya, amma ba zanyi haka ba saboda in nayi haka to nasan wata rana ni zaka farmaka." Zaro ido yayi da matuk'ar alamun tashin hankali da yanda maganar ta sokeshi, mahaifiyata? Take tunanin na...? D'orawa tayi da "Dan Allah daga yau karka sake shiga d'akin, bana buk'atar gaisuwa ko samun girmamawa daga gareka, sannan ka fita harkar Hamna, karka nunawa kowa wani abu ya shiga tsakaninku, inba haka ba kuma har ni za'a tsine ma a gidan nan, dan Allah ka min wannan alfarmar." Rintse ido yayi sosai hawaye wasu na bin wasu, yana kallo ta fita ta bar d'akin yana kuka kamar yaro na goye, ranar dai kamar yanda masu hidima basuyi bacci ba haka ma Hamna da tasha d'inki tana ta wani sabon kukan Ummy na rarrashi, Ammar ma kwana yayi yana kuka yana ji kamar ya kashe kanshi, amma tunani biyu ya hanashi aikata hakan, na farko ba shi ba rahamar ubangiji, na biyu kuma mahaifiyarshi yana da yak'inin ba zai samu addua'r ta ba ko bayan ba ranshi, dan haka ya bawa kanshi hak'uri sai dai kalamanta sun matuk'ar tsaya masa a rai fiye da kima. *Washe gari* yan makaranta sun so su zauna wai tunda ana biki gidansu, amma aka ce su tafi har su dawo, Jamila da Umaimah ma drebansu ne ya aje kowace wajen sagbarta, tun a d'aki Amna ke faman yi wa Hamna magana amma tayi shiru, yanzun fa suna fitowa tace mata "Hamna yau fa a motonki zamu tafi dan ni nawa baida isashen lafiya." Shiru ta mata ta wuce kawai tana sauka daga matakala, Amna da zuciya sai tayi hushi ta taho da sauri ta wuce ta tana fad'in "Kada Allah yasa ki min magana kiga idan ban rayu ba, ni zaki d'auka yar iska tun daren jiya da kike shigo nake miki magana kin min shiru, aikin banza kawai." Da kallo kawai Hamna ta bita wacce take tafiya da k'yar, dan ko yanzu ma saida tasha gashin jikinta tare da magungunan da Ummy ta bata, duk da auren babban mutum ne kuma a k'urarren lokaci, amma hakan bai hana gidan fara d'aukar hayaniyar jama'a ba tunda harka ce ta masu kud'i, hakan yasa yau Hajia bata falon zaune kowa ya tafiyarshi ba tare daya gaisheta ba, Amna na fita b'angaren samari ta nufa da fad'a mishi zata tafi, Hamna ma na fitowa a farfajiya suka had'u da Ummy suna ta kai da kawowa, tayi bala'in kyau cikin tsadadden leshenta daya dace da kalar jikinta, tarbenta Ummy tayi ta shafa fuskarta wacce zaka fahimci yanayin damuwa da kuka a tare da ita, cikin sanyin jiki Ummy tace "Hamna har yanzu kina jin ciwo ne?" Idan tace a'a k'arya tayi, idan tace eh ma k'arya ta fad'a, dan haka kawai tayi shiru tana kallon k'asa, wasu hawaye ne sukayi barazanar taho mata ta dafata tace "Kiyi hak'uri kinji Hamna, insha Allahu zai bari, yanzu ki saki fuskarki dan Allah ki d'anyi fara'a, duk da nasan dai an rabaki da farin cikinki kenan har abada, amma...Hamna kiyi hak'uri dan Allah dan annabi, ki yafe mana." Haka Ummy ta k'arasa maganar da fashewa da kuka, jin ba dad'i yasa Hamna kallonta ita ma idonta jawur tace "Dan Allah Ummy ki daina kuka kema, Ummy ba kiyi min komai ba wallahi, ba komai zanyi murmushi, kin gani?" Kallonta tayi ita ma tayi murmushin kamar dai yanda tayi sannan tace "Ki kula da kanki kinji, ku je Allah ya bada sa'a." Wucewa tayi ta nufi wajen motonta, sai dai ina tana hawa taji wani bala'i daga k'asanta kamar ana sukarta saboda d'inkin da aka mata, sauka tayi kawai ta fita daga gidan ta samu adaidaita ta hau. Amna ma na shiga sallama tayi amma shiru, Jamil dake shirin fita ne ya amsa mata suka gaisa kafin tace "Yah Ammar yana ciki ne?" Cikin rashin sani yace "Eh to, gaskiya ban sani ba, amma bari na duba miki." K'wank'wasa k'ofar yayi tare da "Yah Ammar, kana ciki kuwa?" Ammar daya ji buga k'ofar ya taso ya bud'e dan k'ok'arin kawar da damuwarshi, Amna dake tsaye a bayansu kawar da kanta tayi dan tun towel d'in nan na jiya ne a jikinshi, juyowa Jamil yayi yace "Ga mai son ganinka can." Kallon Amna yayi wacce kanta ke kallon wani wurin, ficewa Jamil yayi shi kuma ya kafeta da ido, jin shiru yasa ta d'an sunkuya tace "Ina kwana yah Ammar." Cikin wata irin murya yace "Amna da wata matsala ne? Ko makaranta zaki tafi?" Ba tare data kalleshi ba tace "Eh yah Ammar, dama na zo ne na fad'a maka." Cikin matuk'ar sanyin jiki yace "Ok kije kawai, Allah ya bada sa'a, ba zan fita ba yau dana sauke ki da kaina." Saida ta d'ago ta kalleshi saboda mamakin yanda yake mata magana cikin taushi kamar ba shi ba, jinjina kai tayi tace "Ba komai yah Ammar, sai anjima." Juyawa tayi ta fita ita ma akan motonta ta tafi duk da yana da yar matsala, yayin da shima ya koma ciki ya sake kwantawa ya duk'ufa tunani, yana haka kiran Hajia ya shigo wayarshi, bugawar zuciyarshi ne ya tsananta yayin da gabanshi ya fara dukan tara tara, me zaisa Hajia ta kirashi bayan rabon daya ga kiranta a wayarshi tun yana France, shima idan tana son ya aiko mata da wani abu ne, mik'ewa yayi jiki a sanyaye ya zauna yana ci gaba da kallon lambar, saida kiran yayi daf da tsinkewa kafin ya d'auka ya d'ora a kunne yayi shiru, cikin yanayin rashin mutumci tace "Sai kaga dama zaka d'aga wayar ko?" Shiru ya sake mata kafin tace "... *Insha Allah page 25 sai nan da wani lokacin idan Allah ya bud'i ido lafiya, ina buk'atar addua'r ku.*👏 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _25_ "Tv ta nake buk'ata ka kawo min yanzu yanzun nan, idan kuma ba haka ba wallahi sai nasa ubanka ya siyo min tv guda goma ya zube min su gabana." Tana gama fad'a ta kashe wayar, lumshe ido yayi tare da sauke ajiyar zuciya, aje wayar yayi gefe ya mik'e a kasalance ta fad'a bayi dan yin wanka, bai wani d'auki lokaci ba ya fito ya shirya cikin shadda kalar chocolat da tasha d'inki da chocolat zare had'e da kalar ruwan madara, ba hula a kanshi sai takalman kalar ruwan madara da agogo duk da dai tafi takalmin haske, turarenshi ya d'auka *Dolby* ya fesa kafin ya d'auki wayarshi da makullin d'aki dana mota ya fito, kai tsaye wajen aje motoci ya nufa ya kuma bar gidan, saida ya fara siyan sabuwar tv a wajen wani daya sani ya bayar a kai gidan kafin ya wuce asibiti. Sunyi mamakin ganinshi da safe a asibiti dan duk ranar juma'a sai k'arfe *02:00* yake shiga ofishinshi, yana zuwa ya shiga ciki ya rufe da makulli ya zauna, take abubuwan da suka faru jiya suka shiga dawo masa a kai, cikin zuciyarshi ya tambayi kanshi da "Ko a wane hali take yanzu? Ta tafi makarantar ne? Shin zata iya jarabawar ma?" Ta wani b'angaren kuma tunanin tattunawarshi da mahaifiyarsu yake, ya aunty Hadiza zatayi idan tasan abinda ya faru? Da wane ido zai kalleta ya mata bayani? Wace irin d'auka zata mishi? Wannan tunanin shine suka tayashi hira har tsawon wani lokaci, yana cikin wannan tunanin agogon dake jikin bangon ta sanar dashi k'arfe *12:00* daidai na rana, sosai ya jima yana mamakin yanda lokacin yayi sauri haka, a hankali ya mik'e ya d'auki makullan ya fito, ba tare da kula kowa ba ya fice duk da likitocin na gaisheshi da girmamawa, yana shiga motar gida ya koma da niyyar kwantawa, amma yana shiga a wajen aje motocin ya samu mata zaune harda Ummy ma a cikinsu, fitowa yayi a raunane yana kallonta amma tana d'aga kai suka kalli juna ta wurga masa harara tare da had'e rai, takowa ya farayi da niyyar yau dai zai gaisheta harda ma k'awayen ta, amma Ummy na ganin ya nufesu ta mik'e kamar wacce aka tsikara ta nufi hanyar falon Hajia, cak ya tsaya yana kallonta da matuk'ar rauni a tare dashi, tahowa yayi da niyyar shiga b'angaren su saiya hangi Amar ya fito daga falon Hajia, baiyi mamakin ganinshi ba dan duk samarin suna zuwa gida dan shirin zuwa masallaci, abun daya sosa zuciyarshi shine ganin Ummy tare dashi tana ta faman b'alla masa botiran rigarshi ta shadda wacce ke nuna yayi shirin zuwa masallaci da d'aurin auren babansu, da kanta ta karb'i machette d'in shi ta saka mishi tare da gyara masa zaman hula, cikin gaggawa Amar ya wuce yana fad'in "Ummy sai mun dawo." Hannu ta d'aga masa tana fad'in "A dawo lafiya shalelen Hajia." Wani murmushi Ammar yayi da shi kanshi baisan manufa ko fassararshi ba tare da juyawa ya koma motarshi, zai tayar Amar ya k'araso ya buga gilashin motar, saukewa yayi ba tare daya kalleshi ba shi kuma yace "Wai har ka shirya ne?" D'ago ido yayi ya kalleshi take kuma ya d'auke idonshi, a haka Amar ya sake cewa "Ammar Abba fa yace muje da wuri masallacin, kuma kai na ga yanzu ga shigo." Tayar da motar yayi yana cikin d'aga gilashin shi yace "Tunda dai kaje ai ba sai naje ba." Yana fad'a yayi baya baya ya daidaita hancin motar kan k'ofar fita ya fice, girgiza kai Amar yayi shima ya shiga tashi motar ya fice. Tun a hanya ya saka a ransa zai ci gaba da zama a yanda yake, Ammar d'in sa, ba zai bari wannan damuwar ta canza shi ba, tunda dai ba zasu fahimci nadamarshi ba bare su bashi damar neman gafararsu, to kawai zai nuna kamar babu wani abu daya faru, sannan ya murje idonshi ya kalli kowa kamar yanda yake kallonsu a baya, da wannan ya isa makarantar su Hamna wanda ya samu d'alibai nata fitowa daga cikin makarantar, ta cikin gilashi ya k'urawa k'ofar ido yana jiran fitowarsu. Amna ce ta fara fitowa akan motonta tana shirin hawa titi, oda yayi da k'arfi wacce tasa ba ita ba har wasu saida suka juya suka kalli wajen, tana ganin motar k'irar Honda bak'a wulik ta tsaya, sake juyowa tayi ta dawo kusa da motar ta kashe moton ta sauko ta zo daf dashi, sauke gilashi yayi ya k'ura mata dara dara idonshi ta cikin farin gilashinshi wanda ke zagaye da maroon d'in kala, saida ya shafa gemunshi kafin yace "Ina kankana?" Nuna masa k'ofa tayi cikin taushin murya tace "Tana kan hanyar fitowa." Mayar da idonshi yayi kan k'ofar yace "A motonta ta zo ita ma?" A hankali ta girgiza mishi kai alamar a'a amma ba tace komai ba, dan ta tuna in sunyi fad'a da Hamna shi ke musu dukan tsiya ya musu sulhu, tana kuma tsoron ya tozartasu cikin mutane akan hanya shiyasa tayi shiru, shirun yayi kamar yanda tayi ba tare daya daina kallon k'ofar ba, ita ma kafe k'ofar tayi da ido har suga fitowar Hamna tare da k'awarta Farida, ba tare daya kalli Amna ba yace "Kirata." Da sauri ta wuce dan cika umarninshi, gabanta tasha fuska a d'an had'e tace "Wai ki zo inji yah Ammar." *Ammar*, wannan sunan da taji ne yasa gabanta zubewa ya fad'i, yayin da zuciyarta ta shiga harbawa da sauri kamar zata fasa k'irjinta ta fito, yake kiranta? Akan wane dalili kenan? Me zai mata kuma bayan duk abinda ya faru? Rashin sanin amsar yasa ta kalli Amna ita ma rai a b'ace tace "Ki ce masa ba zan zo ba." Ita ma cikin hassala tace "Ba zaki zo ba fa kika ce? Yah Ammar fa nace miki yake kiranki." A harzuk'e tace "Eh shi d'in, ubana ne da ba zan fad'a masa haka ba? Ke dai da kika ji zaki iya sai kije amma banda ni." "Me kike nufi? Hamna karki fad'a min maganar banza mana daga yar k'aramar magana, ni d'in naji zan iya kuma zan tabbatar miki da haka, zan kuma juya na fad'a masa kince ba zaki zo ba, watak'ila shi ya zo da kanshi kinga sai ranki ya b'ace a banza." Cikin rashin damuwa tace "Eh kije ki fad'a masa d'in, ya jima bai zo ya yanka ni ba." Amna ta juyo da niyyar tafiya ta ga ya bud'e k'ofar ya zuro k'afa d'aya, cike da wani tako na isa da k'asaita kamar sarki ya fara takawa zuwa gabansu, tsayawa Amna tayi tana kallonshi gabanta na fad'uwa na abinda zai faru, haka ita kanta Hamna gabanta fad'uwa yake dan tasan k'aramin aikinshi ne ya mata akuyanci, yana k'arasowa fuskar nan kamar baisan sunan wani abu dariya ba, Amna ya kalla ya tara mata hannu yace "Makullin motonki?" Hannu na rawa ta mik'a masa makullin a zuciyarta tana fad'in "Yau kuma wak'i'ar harda moton zata shafa." Wannan k'awar ta Hamna ya bawa makullin moton ba tare daya kalli k'wayar idonta ba yace "Kije dashi, zata je ta d'auko." Ita kanta Farida jiki na d'an rawa ta karb'a yayin da ta kasa kallon fuskarshi saboda kwarjinin daya mata da kuma tsoron al'amarin shi, Amna ya kuma kallo yace "Wuce mota mu tafi." Kallonshi tayi ta kalli motar ta kuma kalli Hamna kafin ta wuce tana waiwayen bayanta, sai lokacin kad'ai ya sauke idonshi a fuskar Hamna, gani yayi ta mishi wani haske sai idonta da zaka gane tayi kuka, motsa labb'anshi yayi a hankali ta hanyar fad'in "Shiga mota kema." Saida ta kalli idonshi cike da tsanarshi ta d'aga murya tace "Ba zan je ba nace, kai mugu ne, nasan me zaka min yanzu ma idan na bika." Take ya lumshe idonshi tare da bud'e su akanta cikin wani irin yanayi da saida ta d'an tsorata, kallon Farida yayi wacce har yanzu ke tsaye bata tafi ba, yana kallonta taji gabanta ya fad'i da sauri ta kalli Hamna tace "Sai anjima besty." Da kallo ya bita har ta hau moton ta tuk'a ta wuce, Hamna na ganin haka ta fara takawa da nufin tarar adaidaita, bata shirya ba taji ya finciko hannunta ta cikin hijabinta ya rik'e gam, janta ya fara yi ya nufi motar da ita da k'arfi, d'aya hannunta tasa tana son ta k'wak'ule hannunta amma ina, wata zuciyar ce tace mata "Da zaki iya k'watar kanki aida kin k'wata jiya, rik'on da yayi miki jiya shine yasa fa kila kasa katab'us harya cika k'udirinshi a kanki." Yana zuwa ya wurgata cikin motar mazaunin baya sai Amna dake gaba, mayar da k'ofar yayi da k'arfi ya rufe kafin ya zauna mazauninshi yaja motar, rufe duka k'ofofin yayi ya fara sharara gudu, kamar mahaukaciya ta fara bubbuga k'ofar tana jijjigawa tana fad'in "Malam ka bud'e min ko, bana son tafiya tare da kai d'in, ko ana dole ne? Wallahi dana had'a hanya da kai gwara na had'a da shaid'an, nace ka bud'e min na fita can kuje duk inda zaku kai da ita bai dameni ba." Ganin ko sauraronta baiyi ga Amna dake jin zafin kalaman da yer uwarta ke jifanshi dasu ita ma ta k'i kulata, sai ta fara saka k'afarta saitin kujerar da yake tana ta turoshi da k'arfin tsiya, duk da a zaune yake amma jijjigar da take masa tasa har saida sitiyari yayi k'ok'arin sub'uce masa, banza ya mata saida ya har dab'e kan titin filin jirgi wurin kamar jeji ya taka wani mahaukacin birki, har Amna dake zaune daidai saida tayo gaba kad'an ya rage kanta ya bugu a motar, da k'arfi ya bud'e murfinshi ya bud'e k'ofar da Hamna ke zaune tana ta hargagi ya bud'e mata, amma tana ganin ya tsaya ya fito tayi shiru ta kama bakinta, yana bud'ewa ya cakumota da hannu d'aya ya figota ta fito kamar kaza, mannata yayi a jikin motar ya matseta sosai cikin b'acin rai da d'aga murya yace "Ke mahaukaciyar ina ce? Ni ne zaki raina? Ni tsaranki ne? Saboda kawai abinda ya faru zaki nemi ki raina ni? To baki isa ba kinji na fad'a miki." Wurgata ya sakeyi cikin motar yana fad'in "Banza kawai." Yanda ya hankad'ata cikin motar taji zafi sosai daga k'asanta wanda har yanzu ke mata zugi, wata k'aramar k'ara ta saki amma bai kulata ba sai Amna data juya tana kallonta, kafin ta mata magana taji ya figi motar da wani sabon gudu ya d'auki hanya, Hamna kam da ke jin azaba sosai dan ko adaidaita data shigo cikin dubara tayi zaman, kasa zaune tayi da kyau sai d'ogala k'ugunta da take, tana d'an cije leb'e tana dafe cikinta. Babu wanda ya sake magana a motar har suka ga ya d'auki doguwar hanyar madarounfa, sabo kuma dogon titin nan ya samu yana ta raraka ba ji ba gani da kuma gudun tsiya, Amna dai na son tayi magana amma tana jin tsoro, Hamna da abun duniya ya dameta ne cikin zubo da k'walla ba tare data kalleshi ba tace "Dan Allah ni ka sauke ni anan na koma gida ko a k'afa ne, bana jin dad'in zaman nan fa gaba d'aya." Amna ce ta juyo ta kalleta tace "Baki da lafiya ne?" Cike da tausayin kanta tana zubo da k'wallan tace "Bana da lafiya, kuma shima ya sani." Wani irin fad'uwa gabanshi yayi da sauri ya kalleta ta madubi, amma sam bata kalleshi ba sai cije baki da yaga tana yi, k'ala baice ba ya ci gaba da tuk'inshi, suna haka Hamna tace "Nifa bawali nake ji." Da k'arfi ya juyo ya kalleta lokaci d'aya kuma ya kalli gabanshi, ba alamar wasa ta sake cewa "Wallahi fitsari nake ji." Saida tayi tafiyar minti biyu kafin ya samu wuri ya paka motar, aje jakarta tayi ta fito ta duba da kyau ta samu wuri, matsawa tayi nesa dasu zata tsugunna taji ya bud'e murfin motar ya fito, da sauri ta mik'e tana kallonshi cike da raini, gurin yaje yana dube dube kamar yana neman wani abu mai daraja daya rasa, fuska a had'e ya kalleta yace "Ki hak'ura da fitsarin nan ki koma mota." Shek'ek'e ta kalleshi tace "Ban gane ba? A matse nake fa." Tsawa ya daka mata yace "Nace ki koma ko? Ba zakiyi fitsarin a nan ba, ke ba dan ma baki san ciwon kanki ba har nan kinga gurin da zaki iya tsugunawa da abinda yafi komai mahimmanci a tare dake, baki tunanin abinda zai faru dake?" Saida ta harareshi sama da k'asa taja tsaki ta wuce tana fad'in "To meya rage min yanzun? Ko ka manta jiya ka fatatakashi." Ba wai abinda ta fad'a bane ya tsaya mishi a rai kamar tsakin data masa da harara, sai yaji ya gamsu da mace na iya raina namiji inhar ta ganshi tsirara, wata zuciyar tace mishi "Amma ai kai bata ganka ba, wacce idonta ke rufe tana kokawa da kai tana kuka, amma kuma duk da haka lokacin da taji baka da niyyar barinta ai ta bud'a ido ta kalli k'wayar idonka tace " *Dan Allah yah Ammar ya isa haka, na tuba ba zan sake maka rashin kunya ba, dan Allah ka k'yale ni haka na gaji, wallahi kamar zan mutu.*" A hankali ya lumshe idonshi saboda a daidai lokacin ita ma ido ta rufe ruf hawaye na mata zarya a fuska, wata irin shashek'a ce take saukewa mai barazanar tafiya da numfashinta, gaba d'aya jikinta ya saki kamar wacce babu lakka a tare da ita, bud'e ido yayi ya ga dukansu shi suke kallo, cikin mutuwar jiki ya zo ya shiga suka ci gaba da tafiya. Izuwa yanzu kam dukansu sun fahimci wajen mahaifiyarsu ne zai kaisu, sai dai me zasuje yi haka zuwan bazata shine basu sani ba, cikin mintin da bai gaza talatin ba suka isa garin har k'ofar gidan, Amna ce ta fara fitowa ta nufi cikin gidan, Hamna ma fitowa tayi cikin tako da k'yar ta nufi cikin gidan inda ya bita da kallo, saida ya ga shigarsu kad'ai ya tuk'a motar zuwa masallacin juma'a dake garin. Da gudu Amna ta k'arasa shiga da kiran sunan "Mama, Maman mu." Tana zaune kan kujerar k'arfe tana girki a k'aramin gas d'in ta taji muryarta, mik'ewa tayi da murna ita ma ta d'an fito daga cikin runfar zanar da tayi shamaki a wurin, suna ganin juna Amna ta rumgumeta sosai tana farin ciki, ita ma rumgumeta tayi tana fad'in "Auta ta, ke ce haka bazata? Ke da wa?" D'agowa tayi ta juya bayanta da tsantsar farin ciki tace "Tare da Hamna da yah Ammar, shine ya kawo mu." Murmushi tayi ta kama hancinta tace "Kice dake da angon naki ko? Ja'ira kawai ai nasan komai, Ummynku ta fad'a min a waya." Sake fad'awa tayi jikinta tace "Kai Mama, da saura fa." Da d'an mamaki tace "Amma ya akayi kika riga Hamna shigowa? Kullum ita ke fara shigowa da ihun murna, ko dai dan kuna tare da d'an albarka ne yasa ya daidaita mata zama?" Tab'e baki Amna tayi tace "Tace bata da lafiya ne, tun jiya nima na kasa gane kanta." K'arasowar Hamna yasa Hadiza kallonta, yanayin fuskarta ne ya canja lokaci d'aya saboda ganin wani sabon yanayi a tare da Hamnar, hatta tafiya ma da k'yar take yinta alamar tana mata wahala, Amna ce tayi bayan mahaifiyarta su tana bud'a fridge d'in dake kusa dasu ta d'auko ruwan sanyi, Hamna ma na zuwa fad'awa tayi jikin mamansu ta fashe da kuka, wannan abu shi ya d'aga hankalin Hadiza harda Amna dake shirin shan ruwa amma ta dakata tana kallonta da mamaki, cikin rud'u Hadiza ta d'agota tace "Hamna, lafiya? Meye na kuka kuma? Wani abu ne ya faru?" Amna ce tayi saurin cewa "Mama kawai ki rabu da ita iskanci ne, na fad'a miki tun jiya fa take wani basarwa tana share mutane, ba wani abinda ke damunta." Juyawa Hadiza tayi ta kalleta tace "Yi min shiru Amna, akan me zaki ce a rabu da ita? Kinsan me yale damunta ne? Ai kamata yayi ace ke kika fi kowa sanin abinda ke damunta duba da 'yan biyunki ce." Mayar da hankalinta tayi kan Hamna da har yanzu take kuka ta jata suka zauna kan kujerun wurin ta ci gaba da tambayarta, amma sai Hamna ta share hawaye cikin shagwab'a tace "Mama kawai nayi kewarki ne sosai, munfi shekara bamu ganki ba fa, muna so mu zo amma Hajia ta hana mu, na fidda rai da zan ganki sai kawai boss ya kawo mu, dole nayi kukan farin ciki." Dangware mata kai Hadiza tayi tace "Ke dai akwai sakarya wallahi, yanzu akan hakane kika d'aga min hankali." Amna ce ta cire takalmi ta shiga d'akin tana fad'in "Ai dama na fad'a miki iskanci ne." Da kallon jin haushi Hamna ta bita tace "Ke wallahi bana son iskanci kinji ko, ni sa'arki ce da zaki tsaya kina fad'a min abinda kika ga dama?" Daga cikin d'akin tana cire kaya tace "Aje anyi d'in, inba raina mutane ba meye na duk wani canzawa lokaci d'aya? Tun jiya da kika je karatu d'akin Ummy kika zama wata iri dake." Mik'ewa Hamna tayi ta shiga cikin d'akin tana fad'in "Wallahi kika min rashin kunya saina ci ubanki a wurin nan, ina ruwanki da canzawata to? Idan kinji haushi ki fita harkata mana, yar jaraba kai." Daga waje Hadiza tace "Ya isa haka to, kar na sake ji bakin kowa a wurin nan." Amna ce tace "Mama ki rabu da ita ta ci uban nawa mana idan zata iya." Kallon Hamna tayi tace "Ke kinsan ko gawata wallahi tafi k'arfin ki, dan kin rigani fitowa duniya bafa tazara mai tsayi kika ban ba." K'wafa Hamna tayi ita ma ta fara cire kayanta da nufin shiga wanka, kusan a tare suka jero kowace da d'aurin k'irji da zanin Hadiza na atamfa zasu fito hakan yasa suka matse junansu, ture juna sukayi inda Hamna ta bita da harara da tsaki, Hadiza dai na kallonsu tana jin dad'i dan ko ba komai yau tana jin hayaniya a gidanta na yara, Amna ce ta d'auki bokiti ta tara ruwa a bakin panpo inda Hamna ta d'auke kwandon sabulun wankan, Amna ce ta kalli mahaifiyar tasu tace "Mama ki fad'a mata ta ban kwandon nan." Kallonta Maman tayi tace "Hamna ki bata kwandon idan ta fito kya shiga." Cikin turo baki Hamna tace "Wallahi Mama ba zan bata ba saina fara yi, tun a hanya fa tasan ina cewa fitsari nake ji." Hadiza ce tace "To ki shiga kiyi fitsarin ki fito saiki bata wurin." Cikin yanayin sangarta tace "Mama kawai ki k'yalemu kiyi kallonmu, karki sa wannan sakaryar ta raina ni saboda kina d'aukar ta autarki." Hadiza ce tace "To shikenan na saka muku ido, kafin nan ku fad'a min ina yaron kirkin yake ne? Kunce shi ya kawoku kuma banga ya shigo ba har yanzu." Tab'e baki Hamna tayi tace "Waya sanin masa mugun kawai, Allah yasa ma ya tafi ya barmu nan mu kwana." Girgiza kai kawai Hadiza tayi ta ci gaba da duba girkinta, tana kallo Hamna ta damk'i bokitin ruwan tana so ta raba Amna dashi, ita ma rik'ewa tayi sosai tace ba zata saki ba, hakan ne ya janyo musu kokawa da bokitin ruwan har suna ta zubewa a banza, wajen wannan tak'ak'abuwa bokitin ya fad'i k'asa ruwan suka watse a banza, da sauri Hadiza ta lek'o daga yar rumfar tana fad'in "La'ilaha illalahu, wai ku yanzu haka abun naku ya zama? Meye ha...?" Shiru tayi saboda ganin Ammar ya shigo cikin gidan. Amna ce tayi k'asa da kanta yayin da Hamna kuma ta zabga mishi harara ta d'auke kanta, Ammar kam kawar da idonshi yayi daga kallonsu saboda ganinsu kamar 'ya'yan gwarawa, kowace da d'aurin k'irji hallitarsu ta fito fili, ta bayan Amna ya bi ya wuce yana kallon Hamna dake masa wani kallon iya shege, tun kafin ya k'arasa Hadiza ta aje masa kujera tana fad'in "Ammar ina ka shiga? Sun ce kai ka kawosu amma shiru baka shigo ba." Sam babu fara'a a fuskarshi ya zauna akan labb'anshi ya amsa da "Masallaci na tafi Tanti." Da fara'a sosai tace "Haba shiyasa, to anyi sallah lafiya?" Ciki ciki ya amsa da "Lafiya lau." Kallonshi Tanti tayi tana murmushi a zuciyarta tana ayyanawa yau 'yan mulkin ne akan shi shiyasa ko gaisheta ya kasa yi, kallonsu Amna tayi da har yanzu suka kasa sulhunta kansu, girgiza kai tayi tace "Auta, ki barta tayi sai kiyi kinji, ki zo ki kawowa yayanku ruwa yasha kya samu lada ma." Da sauri Hamna ta kalli Hadiza Amna ita kuma turo baki tayi ta sakar mata bokitin tana hararanta, cikin sand'a take takowa kamar wata marar gaskiya saboda ganin yanda Ammar ya had'e rai kamar hadarin gabas, cikin tsoron kar ya daketa ta samu ta shige d'akin ta d'auko hijab ta saka ta fito, ruwa ta d'auko mishi ta zuba ta bashi a lokacin da Hadiza ke tambayarshi meyasa bai tsaya d'aurin auren babban shi ba? Saida ya karb'i ruwan ya d'an kurb'a ya kalli Amna da jajayen ido yace "Wuce d'aki." Kallonshi tayi kamar zatayi kuka cikin muryar tsoro tace "Yah Ammar..dama...alwala zanyi kafin ta fito." Sake wurgo mata idonshi yayi wanda yasa gabanta fad'uwa, dan a yanda suka sani ko gaban mahaifiyarsu ta kama saiya kasheka da mari har ma ya d'auki madaki, ajiyar zuciya ta sauke mai sautin gaske saboda alamar daya mata da ido ta wuce, da sauri ta nufi wajen buta ta zuwa ruwa lokacin Hamna ta shiga wanka, bai sake tankawa ba har saida ya ga shigar Amna d'aki kafin ya kalli Hadiza dake kwashe abinci a kwanuka ya tab'e baki yace "Me yasa zanje d'aurin auren?" Juyowa tayi ta kalleshi ita har ta manta ma data tambayeshi, tun yana k'aramin yaro take k'aunar shi har zuciyarta, ta sanshi tasan halinshi fiye da uwar data haifeshi, hakan yasa bata damu ba saima murmushi da tayi tace "Saboda mahaifinka ne mana, kuma zaiyi farin cikin ganinka a wurin a kusa da shi." Murmushin rainin hankali yayi tare da kallon farfajiyar gidan yace "Ba zan iya wannan abun kunyar ba, tsofai-tsofai da kai kayi wani wai aure, auren ma ba da babbar mace ba ko wata bazawara, yarinya mai k'ananun shekaru, ko ni dake d'ansa wannan yarinyar ta min kad'an na aureta wallahi bare kuma shi." Wani wawan tsaki yayi alamun dai abun ya dameshi sosai, banda dariya ba abinda Hadiza keyi kafin tace "Yaron kirki kenan, amma me yasa kake ganin ta maka kad'an?" Sam babu alamar wasa ko kunya yace "Saboda ba zata iya d'aukata ba, zata iya mutuwa tun kafin aje ko ina, sannan ni banga albarkatun dake jikinta ba wanda zasu iya d'ebewa mutum kewa." Murje ido Hadiza tayi ta nuna abun bai wani dameta ba dan tasan halin katob'aran yaronta tace "To dama wacece zata iya da kai yarona? Ai sai yar baiwa, amma fa duk da haka ita yarinyar ta dace da mahaifinku, tunda kaga kai sabon jini ne ka mata yawa, shi kuma an kwana biyu zai iya tafiya da ita yanda ya dace." Cike da jin an fasa mishi kai yayi wani shak'iyin murmushi yace "Hmm; shi ma fa da sauranshi, dan yanzu haka zai iya samo mana cikakken k'ane." Kafin tayi magana Hamna ta fito daga wanka, har tayi alwala bakin panpo ta basu sake magana ba, saida ta zo daf dashi zata wuce ta gabanshi dan hanyar da zata iya sadaka da d'akin ce kawai yace "Tanti ai duk wacce na kwanta da ita na tashi ita ma kuma ta mik'e da k'afafunta, to wannan ita ce daidai dani saboda ni jaruma nake so ba raguwa ba." Da k'arfi Hamna ta kalleshi amma kash kamar ma baisan da tsayuwarta a wurin ba, cikin murmushi Hadiza tace "Zaka sameta mai jarumta yaro na, zanyi k'ok'arin ganin haka ta faru ko saboda jin dad'in ka." Juyawa tayi ta kalli mahaifiyar tasu dake ta harkar gabanta, sake juyowa tayi ta kalle shi tayi k'wafa ta wuce, zata shiga ciki taji ya sake cewa"Kankana." Cak ta tsaya ta juyo tana aika mishi wani mugun kallo, kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "... *Alhamdulillah Allah*👏 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _26_ Kallonta yayi ya gyara zama tare da shafar gemunshi yana dariyar iskanci ya kashe mata ido d'aya yace "Fita zanyi yanzu, zaki sha kankana ne na taho miki da ita?" Sama da k'asa ta harareshi taja dogon tsaki ta wuce d'aki, ba tare daya daina murmushin ba ya bita da kallon *zaki gane kurenki*, Hadiza ce ta juyo ta bita da kallo tace "Ke Hamna lafiyarki kuwa? Meye na tsakin daga abun arzik'i? Bana son iskanci kinji na fad'a miki, wannan ba yayanki bane? Ko dan kinga yau ya sakar muku fuska ne." Mik'ewa yayi tsaye yana gyara zaman doguwar rigarshi yana fad'in "Tanti ni zan fita na dawo." Kallonshi tayi cike da kulawa tace "A'a, ka zauna mana ka ci abinci saika fita, nasan dai yanzu bakin ruwa zaka je ko?" Murmushi kawai ya mata ya nufi k'ofar fita, da kallo ta bishi a ranta tana mamakin wani sauyi data gani a tare da shi tana fad'in "Yau Ammar babu saurin kai duka, har Hamna ta mishi tsaki amma ya nuna ko a jikinshi, lallai yau farar juma'a ce, ba dan haka ba ai da sai dai ta jiyo ihunta a d'akin." Wata zuciyar ta fad'a mata "Dama ai yau da gobe sai Allah, mutum yana canzawa kamar yanda zamani ke canzawa." Ba tare data daina kallonshi ba tace "Ko kuma dai dan za'a had'a shi da Amna ne, tabbas ma hakane, watak'ila kunyarta yake ji yanzu saboda sun zama surukai." Bata gushe daga tunanin ba taji muryarshi cikin d'aga murya yana fad'in "Mutumin ya kake?" Da kallo ta bisu ganin shi da mai gidan nata suna gaisuwa irinta yaran zamani marasa jin magana, murmushi kawai take saboda yanda suka birgeta kamar wani d'a da uba, dawowa sukayi ciki har cikin runfar inda Shu'aibu ya kama hancin Hadiza yaja sosai yana mik'a mata sallayar hannunshi yana fad'in "Matanmu ya aiki? Ashe bak'i kikayi bayan tafiyata?" Hadiza data saba take kuma jin dad'in zama da mijin nata murmushi ta masa tace "Sannu da zuwa, bak'i kuma ba bak'i ba kam." Ammar da soyayyar dattawan ke birgeshi sagala hannunshi yayi a kafad'ar Shu'aibu ya ja hancinshi yana fad'in "Duk ka jaye mana hanci uwa har yayi tsayi kamar karas, ka canza wani salo mana." Shima kama wuyanshi yayi suna dariya yace "Uwar ka dai ce ka shammata bani ba ja'iri kawai, kuma ma wani salo zan canza bayan na saba da wannan." Kashe mishi ido d'aya yayi yace "Muje waje zan fad'a maka irin wanda zaka sauya." Hararan wasa Shu'aibu ya masa yace "Me yasa sai mun fita? A sani na dai baka jin kunyar fad'an komai ko a gaban wa." D'ora kanshi yayi a kafad'ar Shu'aibu tare da jawo rigarshi yana rufe ido wai kunya🙄🤔 (bala'i, ban tab'a gani ba), cikin nuna jin kunya yace "Nima bansan ya akayi ba yau na ji na sauya, kawai dai muje waje na fad'a maka sabon yayi." Ture shi Shu'aibu yayi daga jikinshi ya kalli Hadiza da banda dariya da girgiza kai babu abinda take yace "Wai ina yan biyuna ne ikon Allah? Amma dai banda Hamna aka zo ko?" Hadiza ce tace "Har da ita ko, yau dai matsiyata ne bisa kanta shiyasa, dan da farko data shigo ma kuka ta saka mana, duk ta canza dai tayi wata iri." Daga cikin d'akin cikin taushin murya Amna "Kawu ina wuni." Cikin sakin fuska ya amsa da "Lafiya lau yan biyu ikon Allah, amma wace tayi magana? Kinsan ban cika gane ku ba har yanzu." Amna ce tayi dariya zatayi magana Ammar yace mishi "Ba kankanar bace, d'ayar ce." Kallonshi Shu'aibu yayi yace "Kai kam dama ai ko mahaifiyarsu ba zata nuna maka saninsu ba, Allah ya maka wannan baiwar tun haihuwarsu." Murmushin jin dad'i yayi ya shafo gemunshi yace "Da wayona fa akayi auren Tanti da Tonton, sannan tare da ni tanti ta ci amarcinta, tare dani tayi laulayin cikinsu, hasalima ni nake shafa cikinta ina fad'a mata zata haifi yan biyu kamar ni da d'an uwa na, sannan a idona ta fara nak'udarsu ni ne ma na kira mutanen gida aka kaita asibi, tare dani akayi jegonsu, sannan tare da ni Ummy ta rainesu har sukayi wayo, to ni kam meye zai shige min duhu a tare dasu?" Duk da Shu'aibu ya ji kishi a zuciyarshi lokacin da Ammar yace sun ci amarci, amma kuma bai nuna ba ko a fuska sai darewa da yayi yace "Gaskiyar kam, amma yanzu dai bari na gano kankanar ta bakinka." Zai shiga d'akin Ammar ya rik'o hannunshi yace "Muje waje haba muyi hira, rabu da kankana nasan matsalarta." Daga d'aki Amna tace "Kawu sallah ma take." "Shiyasa dai banji muryarta ba ashe." Cewar Shu'aibu kafin ya kalli Hadiza yace "Idan kin gama abincin ki aiko mana shi k'ofar gida, wannan sarkin zancen ba zai barni na gama kallonki ba." Dariyar shak'iyanci yasa suka nufi waje yana fad'in "Ai mutumina shiyasa nake so muje waje na k'ara baka wasu shawarwarin yanda zaka ci gaba da kula mana da tantinmu, dan naga ba tsufa kuke ba ku, shiyasa nake so naga kullum kana nan a jaruminka kana bada wuta a ciki." Shu'aibu dariya yayi yace "Cikin me?" Sunkuyar da kai yayi yace "Kai ma dai har saina fad'a? Ka sani mana." Shu'aibu ne ya d'auki tabarma suka fita, suna zuwa ya shinfid'a a k'ark'ashin bishiyar dake k'ofar gidan tare da wata k'atuwar darduma suka zauna, a cikin gida kuma Hadiza k'walla kiran Amna tayi tana fitowa tace ta d'auki abinci ta kai musu, cikin ladabi ta d'auka har da ruwa ta kai musu. *Gaga's House*😍 Hankalin Ummy ne ya fara tashi ganin babu Hamna kuma babu Amna, wayarta ta fara kira amma abun mamaki saita samu wayar a d'akinta, alama dai wahalar da tasha tasa ta manta da wayar ma a d'akinta, Amna ta koma kira ita kuma kashe wayar dan tunda zasu shiga aji ta kashe oga boss kuma yasa ta manta bata kunna ba, saida rana tayi sosai lokacin su Hamna na cin abinci ta d'auki wayar ta kunna, ganin kiran da Ummy tayi bata samu ba yasa ta mayar da kira, da sauri Ummy ta d'auka tana fad'in "Amna, lafiyarku k'alau kuwa? Ina kuka tsaya ne haka?" Da murmushi a fuskarta tace "Ummy kiyi hak'uri banga kiranki ba sai yanzu na kunna wayar, wallahi muna lafiya lau babu komai." "To kuna ina har yanzu baku zo gida ba?" Ta fad'a cike da k'aguwa, kallon Hamna tayi da ita ma ke kallonta tace "Ummy gamu nan gida wajen Mama." Da k'arfi Ummy ta zaro ido tace "Me? Mamanku? Ke da wa?" Jin yanda Ummy ta rud'e yasa tayi dariya tace "Ummy kwantar da hankalinki, yah Ammar ne ya kawo mu tare da Hamna muke." Da sauri cike da tsoron abinda Hamna zata fad'awa mahaifiyarta Ummy tace "Ina Hamnar take? Bani ita." Mik'awa Hamna wayar tayi ta ci gaba da cin abincinta Hamna kuma ta amsa da "Ummy lafiya lau muke fa." Ajiyar zuciya ta sauke tace "Hamna ina cikin damuwa sosai, kar Hadiza ta fahimci wani abu ya faru dake, dan Allah ku dawo yanzu Hamna kafin Hajia ta ankare da rashin dawowarku, kinsan a kaina k'urar zata sauka tace da sani na kuka tafi babu izininta." Cikin rashin karsashi Hamna tace "Ummy wallahi ba laifinmu bane, kawai muna fitowa daga makaranta ya zo ya d'auke mu da k'arfi." Cikin rashin kulawa Ummy tace "Ni ban damu da lamarinshi ba, ko da kun dawo ma yasan yanda zaiyi ya fitar da kanshi wajen Hajia ko kuma ya sake tsula mata wata tsiyar, ku kawai nake ji Hamna, dan Allah ku k'ok'arta ku dawo kafin sallah la'asar, kunga gida anata hidima kuma ana tambayar ina kuke." Cikin sanyin murya tace "Ummy yanzu ba zamu iya kwana a nan ba? Mun jima fa rabonmu da nan." Da sauri tace "A'a Hamna rufa min asiri dan Allah, ni dai na rok'eku ku dawo yanzu kinji, inba haka ba ni zan zo garin na taho da ku, Hamna ko kin manta kina buk'atar kulawa ne?" Turo baki tayi kamar tana gabanta tace "Shikenan Ummy zamu dawo." Murmushi tayi mai sauti tana fad'in "Yawwa yar albarka, sai kun zo kinji, ina maman taku ne?" "Tana waje." Cewar Hamna a dak'ile kafin Ummy tace "Bani ita mu gaisa." "To." Ta fad'a tare da mik'awa Amna wayar tace "Kaiwa Mama." Figar wayar tayi tana dalla mata harara da fad'in "Ke musaka ce da ba zaki iya tashi ba ko me?" K'ala ba tace mata ba har ta fice ta kaiwa Mamansu wayar, sosai suka gaisa inda Hadiza take sake godewa Ummy kan kula mata da yaranta da take, sannan ta d'ora da "Munji kuma abun alkairi had'in da Hajia tayi, Allah ubangiji yasa alkairi yasa ayi muna raye." Ummy ce ta amsa da "Ameen, insha Allahu ma ai zan zo ko dan muyi magana da shirye shiryen abinda ya kamata na bikin, ina jira ne a gama wannan sabgar lokacin an kawo komai da komai sai na zo." Ita ma Hadiza murmushi tayi tace "Sa'ada kenan, ai ke ce uwar yaran nan, duk abinda kikayi wallahi d'aya ne, babu abinda zan ce muku ke da lieutenant ai sai godiya." "Ba komai wallahi yiwa kaine ai." Da haka sukayi sallama ta mayarwa da Amna wayar d'aki wanda ta same su suna rigima Hamna ta dage sai Amna taje waje ta fad'awa Ammar Ummy tace su tafi, ita kuma tace ba zata ba salon ya mata rashin mutumci, dariya Hadiza tayi tace "To ke da zai aureki kina shakkar yi masa magana tun yanzu, ya kenan idan anyi auren?" Hamna ce tace "Sai ya raina ta mana ya juyata yanda ya ga dama." Hararanta tayi tace "To ina ruwanki idan ya juya nin? Ai ba ke ya juya ba ko? Kuma dama haka ake so mace ta zama k'asan mijinta." Wata dariyar shak'iyanci ta mata tace "Lallai ma yarinya, to ki zama k'asan wannan mahaukacin, wallahi wata rana saiya saki kin lashe tafin k'afar shi." Cikin jin haushi tace "To sai me idan na lashe? Ai k'afar mijina ce." Hadiza ce tace "Kinga ku bar rigimar nan tashi kije ki fad'a masa." Mik'ewa tayi ta fito ta wanke hannunta ta d'auki hijabinta ta saka ta fita rai a b'ace, data same shi ta fad'a mishi cewa yayi sai bayan sallah la'asar zasu tafi dan haka su jira, ba tace komai ba face to ta dawo ciki. *A can gida* kuma ba laifi ana ta bikin lieutenant da Zeituna, anci an sha sosai ana gwangwajewa, kuma daga Ummy har lieutenant babu wanda ya damu da rashin kasancewar Ammar a wurin hidimar, a wurinsu ma hakan ya fi musu kwanciyar hankali a madadin yana nan d'in, rana tsaka babbar mota ta paka k'ofar gidan aka fara shiga da kaya ciki, saida aka shiga dasu tsaf farfajiyar gidan sannan suka nemi inda za'a zuba, Zeinabu ce ta tambaya daga ina suke suka ce Alhajin gidan ne ya aiko su, Hajia suka fad'awa inda ta kira Alhaji ta tambaye shi kayan meye? A cewarshi na amarya ne a ware d'aki na musamman a zuba mata a ciki, nan aka ware mata d'aki ita ma a falon k'asa aka shiga da kayan ciki, Alhaji ne ya umarci Zeinabu da Soueiba su jagoranci al'amarin a gyara d'akin, ba b'ata lokaci suka shiga gyara tare da taimakawar mutane dayawa, cikin k'ank'anin lokacin saiga d'aki ya d'auki saiti sai zuba k'amshi, Hajia data shigo ganin gyaran ranta ya b'ace sosai, dan kayan daya zuba mata ba kad'an bane ba kuma masu arha ba, tana al'ajabin yanda yar aikin gidanta k'azama zata shigo gidan nan a matsayin matar baban d'anta, haka dai aka rufe d'akin ana jiran lokacin da mai shi zata shigo. Sai bayan sallah la'asar ne Hajia ta fahimci rashin ganinsu Hamna da batayi ba, ta so tambayar Ummy ina yan rainonta suke, amma kuma daga ita har Ummy d'in suna tare da bak'i, hakan yasa tana cin karo da Jamila a falonta ta kalleta tace "Ke ina su Hamna suke?" Da d'ard'ar tace "Eh to Hajia wallahi nima ban sani ba, tunda safe rabona da su." Kallon tuhuma ta mata tace "Amma ai jarabawarsu sauka d'aya ne ake ko?" "Eh Hajia." Ta fad'a kanta k'asa, a kaikaice tace mata "Ki kira min shalele a k'ofar gida." "To." Ta fad'a tana fita daga falon, a k'ofar gida ta samu Amar tare da abokanansu da duk samarin gidan suna ta hira da raha, sallama tayi suka amsa kafin ta d'ora da "Ina wuni." Jibril daya kafeta da ido duk yaji haushinta ya cika mishi zuciya saboda masha Allah d'inkin dake jikinta ya bi k'irarta sosai tare da fito mata da komai, kuma wani gyale ne ta sab'a a kafad'a wanda dashi gwara babu, amsawa sukayi inda shi kuma ya bita da harara, suna had'a ido ta k'ura mishi ido tana mishi kallon mamakin meye na harara kuma? Bata d'auke idonta ba taji yace "Me kike nema anan kuma?" Saisaita kallonta tayi tace "Dama Hajia ce tace na kira mata yah Amar." Amar ne yayi saurin kallonta yace "Ni kuma? Lafiya?" Girgiza kai tayi tace "Ni ma ban sani ba." Juyawa tayi zata tafi Jibril ya bita da kallo, abokinshi ya kalla zaiyi mishi magana sai kuma yaga shima ita yake bi da kallo, wani wurga ido yayi alamar jin haushi tare da zabura daga kan kujerar ya mik'e ya bi bayanta, rufe ta yayi ta yanda ba'a ganinta yana binta har suka shiga cikin gidan, sam a tunaninta Amar ne ke biye da ita ashe ko tahowa ma baiyi ba, k'eyar ta taji an zungura ta baya da fad'in "Ke miye haka?" Juyowa tayi tana dafe wurin ta kalleshi, ganin shine yasa tace "Yah Jibril." Saida ya matsa daf da ita kamar zai had'e ta ya kalli idonta yace "Baki san da maza a wurin bane zaki fito haka babu hijabi?" Cikin rashin fahimtar kalamanshi tace "Ban gane ba yah Jibril? Naga biki akeyi a gidanmu ai..." "Ai me?" Ya katseta da k'arfi har saida ta d'an zabura, nunata da hannu yayi yace "Allah kika sake fitowa waje babu hijabi saina karyaki a wurin nan, maza wuce ciki malama." Turo baki tayi irin na ranta ya b'ace ta juya a fusace zata shige, hannunta taji ya fizgo ya dawo da ita gabanshi ba tare daya saki hannun ba yace "Wa kike turowa bakin?" Kawar da kanta tayi gefe bata daina zunto bakin ba, yatsunshi biyu yasa ya jawo leb'en ya murd'e sosai yana fad'in "Ni kike turowa bakin Jamila, saboda na miki magana kisa hijab shine zaki zage ni." Bud'a idonta tayi da sukayi jawur dasu hawaye suka zubo mata ta kalleshi tace "Wallahi yah ni ban zage ka ba." Sakin leb'en nata yayi yace "To me kikayi kenan? Meye marabar wannan da kika min da zagi?" Jin ya saki bakin nata yasa taja baya tace "Kayi hak'uri to." Juyawa ta sakeyi ta shige har saida ya daina ganinta kad'ai ya koma waje, Amar kuma na zuwa Hajia tace "Ka kira min yaran nan kaji ina suke?" Da kallo ya bita yace "Wane yara kuma?" Fuskarta a sake tace "Su Amna mana, har yanzu fa basu dawo daga makaranta ba, kira min su kaji uban me ya tsayar dasu, naga alama yaran nan suna nema su zamar min yan iska." Cikin rashin jin dad'i ya soma danna wayarshi, da sauri tace "Ka kira lambar Hamna, dan ita ce fitsararriyar cikinsu, duk yanda akayi ita ce zata ja yer uwar koma ina suka tafi." Danna kiran lambar Hamna yayi amma tana ta k'ara ba'a d'aga ba, dan Ummy data ga wayar ma b'oye mata tayi har ta dawo, dole ya kira Amna amma Hamna na ganin kiran tace mata "Kinga idan kin d'aga kice gamu nan kan hanyar zuwa gida, dan na tabbata Hajia ce zata saka shi ya kira mu, kuma nasan ni zata d'orawa laifin ta min tijara, gwara idan mun koma ayi duk wacce za ayi." Hadiza dai dariya tayi inda Amna ta d'aga ta kuma fad'a mishi duk abinda ta fad'a mata, kasancewarshi ba mai son jan magana ba yasa ya kashe wayar ya kalli Hajia yace " Suna zuwa yanzu, sun tsaya bitar jarabawarsu ne ta gobe kasancewar lissafi zasuyi." Yana fad'a ya juya zai fita tace "Shalele ka jira yanzu za'a kawo muku abinci." Uhum bai ce mata ba ya fice, Hadiza data saka su Hamna gaba suna tattaunawa irin na mahaifiya da 'ya'ya, umartarsu tayi da su shirya tunda anyi sallah, haka kuwa akayi suna gama shiryawa Ammar ya shigo tare da Shu'aibu, sallama sukayi cike da kewar juna suka d'auki hanyar komawa gida, yanzun ma Amna ce gaba sai Hamna a baya, yanzu ma cikin mintin da bai gaza ashirin da wani abu ba suka iso saboda yana gudu sosai. D'akinsu suka wuce ba tare da kowa ya lura da su ba suka shiga shiryawa suma, yamma tayi sosai suka gama suka fito, lokacin ne akasan da zuwansu gidan, Ummy har d'aki ta shiga da Hamna ta k'ara duba lafiyar jikinta, ana sallah magrib Hajia ta hangesu farfajiyar gida suna d'aukar hotuna tare dasu Umaimah da Jamila, k'anwar Jamila mai bi mata *Nazeefa* ta turo ta kira su inda ta e su sameta a d'akin ta, dukansu babu wanda jikinshi baiyi sanyi ba tare da tsoron abinda zai faru suka nufi d'akin nata. A tak'aice dai fad'a da masifa da bala'i babu wanda basu gani ba, saida tayi ikrarin idan haka ta sake faruwa to su kuka da kansu, suna fitowa suka ci gaba da harkokinsu kamar kowa tunda dama sun saba da irin wannan tijarar, anyi sallah isha'i ana ta shirin tarban amarya Ammar ya shigo falon Hajia, duk da kowa na hada hadar gabanshi amma ganin Ammar da wasu manyan kwalaye har biyu yasa kowa ya tsaya dan kashe k'wark'watar idonshi, gaban Hajia wacce ke zaune cikin manyan tsofaffin mata k'awayenta ya diresu, juyawa yayi ya fita bayan wani lokaci kuma sai gashi da manyan salkar goro ha guda biyu ita ma, ajewa yayi gabanta kafin ya kalli idonta yasa hannu aljihun wando ya fito da babbar enveloppe, mik'a mata yayi tare da fad'in "Hajiar mu ga lefena na kawo, ga kud'i na tambaya da gaishe da iyaye da duk wata bidi'a, sadakin kuma sai ranar d'aurin aure Alhaji Hassan zai biya." Hajia data saki baki tana kallonshi d'ora k'afad'aya kan d'aya tayi ta kalli Sa'ada dake zaune gefe ko kallonshi ba tayi tace "D'an ki ya rasa yan uwan da zasu kawo mishi kayan ne? Ko kuma dai rashin kunyar tashi ce ta motsa? Shiyasa ya kawo kayan da kanshi saboda ya nuna mana shi kangararre ne." Kallonta Sa'ada tayi cikin taushin murya tace "Hajia kema kinsan halinshi ai, yana so ya nuna rashin kunyarshi a fili ne, sannan ya nuna babu wanda ya isa dashi." Shi ma bai juya ya kalli Ummy ba yace "Banga abun rashin kunya ba anan, k'anwata ce zan aura da muke gida d'aya, saboda kawai na ragewa mutane wahala sai ya zama fitsara?" Enveloppe d'in daya mik'a mata ta karb'a ta jinjinata tana kallonshi tace "Da alama kud'in dayawa, ai banyi tsammanin zakayi k'ok'ari haka ba." Murmushin nan dai ya mata wanda yake mata idan zai b'arkota yace "Hajiata kenan, Amna fa kika bani, tunda kika ga nayi wannan k'ok'arin kisan da cewa ni kad'ai naga abinda na gani." Ita kanta Hajiar wani wawan murmushi ta masa tace "Allah ko marar kunya? Kenan dai jikar tawa tayi ko?" Wannan karan har saida sautin murmushin ya fito kafin yace "Sosai ma, ai ko baki bita da gyara ba nasan zan huta da kayana." Wata dattijuwa ce gefe Hajia tace "Kai fice mana a wurin nan bama son surutun nan na kwankwatsar kwalabe." Dariya suka saka mata inda shi kuma yace "Tsohe ikon Allah, to ku da kun riga kunci naku zamanin, kuma fa kinsan ance kamar *kumbo* kamar *katanta*." Tshohuwar a zuciyarta ta amsa masa da "Tabbas, yanda kayi gadonta wajen kyau da zubin hallita, haka kayi gadon rashin kunyarta da sako zance." Kallonshi Hajia tayi tace "Ina fatan dai uwarka ta fad'a muku irin hidimar dake gabanku? Dan kamar yanda na fad'a ne dole za ayi aure irin auren buzuwa." Hannayenshi ya zuba aljihu yana mamakin yanda ko gaban idon mahaifiyarshi ko bayan idonta ba zata iya cewa mahaifiyarka ko mamanka ba sai dai uwaka, juyawa yayi zai fita yana fad'in "Zanyi komai akan zab'inki ai a shirye nake." Cikin d'an d'aga murya tace "Kace ubanka ne zai biya sadakin? A wane dalili ne kai ba zaka biya ba?" Ba tare daya tsaya ba bare ya juyo yace "Saboda shi za'a haifawa jikan." Ummy ce ta d'aga kai ta bi k'eyar shi da kallo tana jinjina wannan al'amari na d'an nata, kamar ba shine jiya yayi wa yarinya fyad'e a cikin gidan nan ba, kai dole ma su b'oye wannan sirri ita da Hamna, dan ko sun fito dashi shi dai babu ruwa a idonshi bare yaji kunya ko nadama, zai ma iya fassarawa mutane yanda al'amarin ya kasance kad'an ne daga cikin aikinshi, Hajia kuma ko a jikinta sai jawo akwatinan da tayi aka bud'e, sam babu wanda yayi tsammanin da kaya a cikinsu duba da yanda shi kanshi ya d'auko su ya shigo da su, amma abun al'ajabi dukansu guda goma sha hud'u cike suke da kaya masu yawa da kyau, ga kuma goro da kud'i har million biyu rigis, Hajia kam ya birgeta a karon farko na rayuwarta, nan aka manta da jiran amarya ake anata duba kayan nan wasu na d'auka hoto, isowar motocin da suka tafi d'aukar amarya ne yasa Hajia kallon Sa'ada tace "Ki shiga da kayan d'akinki ki ajiye." "To." Ta fad'a tana mik'ewa ta d'auki kayan tare da taimakon k'awayen ta ita ma da suka zo tausar k'irji. *Alhamdulillah* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _*Alhamdulillah Ala ni'imatil islam, Allah nagode maka daka sawak'e min komai, ba yin kaina bane, ba dubarata bace, ba wayona bane, Allah nagode maka, yan uwa kuma nagode sosai da gudummuwarku, Addu'arku ta riskeni a sanda nake da buk'atar ta, haihuwa ta zo min da sauk'i fiye da zatonku, Allah kaine Allah kuma abun godiya, Allah ka raya min yarana ka bani ikon yi musu tarbiya irin ta addinin musulunci.*_👏 *Aci gaba da gashi guy's.*💃 _27_ Ana cikin wannan hidima aka kawo amarya, motoci dai gasu jingim wanda suka paka k'ofar gidan, amma Zeituna bata da dangin da har zasu iya d'aukar motocin, gaba d'aya wanda suka zo rakiyarta basu fi mata ashirin Ba. Kuma a haka wai dangi sun zo ne k'wansu da k'wark'watarsu saboda ta auri mai kud'i, tarba ta musamman suka samu daga gidan girma, inda aka wuce da amarya d'akin ta aka zaunar da ita, saida suka ci suka sha suka k'oshi kafin suka bar gidan tare da yi wa amarya jan kunne cewa karta manta da danginta wajen cin arzik'in, wasu daga cikin motoci aka saka suka mayar dasu gida suka bar amarya da halinta. Kafatanin yaran gidan ne suka baibaye Zeituna suna kallo, wacce ita kuma ta sanda kanta k'asa ta kasa had'a ido da kowa saboda tunaninta duk kallon rashin mutumci suke mata, Hamna da Amna da Jamila ne suka shigo tare sai Umaimah dake bayansu, zaune sukayi inda Umaimah ke fad'in "Ku kuma ku tashi ku fita ku ba mutane wuri duk kun zo kun sata gaba kuna kallo." Nazeefa ce ta kalleta tace "Ai dai ganin amarya muka zo." Cikin tsawa Umaimah tace "Ke dallah tashi ku fita, ba gidan zata zauna ba sai kiyi ta kallonta ai." Kamal ne ya kalli Umaimah ya mik'e tsaye yana zuba hannayenshi aljihu yace "Kaji mace dan Allah zaki kore mu, amaryar ubana ce fa." Kallon juna suka shiga yi dan abun ya basu mamaki, a sanin da suka ma Kamal baya da surutu irin haka, Hamna murmushi suka bishi da kallo har suka fita, sai Jamila da tace "Allah yasa kar mu samu yah Ammar na biyu a gidan nan." "Ameen." Cewar Amna da saurinta, Umaimah ce ta kalli Zeituna wacce k'irjin ta ke dukan uku uku saboda zatonta zasu mata rashin kunya ne shiyasa suka kori yaran, cewa tayi "Aunty Zeituna ki bud'a fuskar ko, yaran sun fita sai mu kawai." K'ara sanda kanta tayi taja gyalenta ta sake rufe fuska ruf, Hamna ce tabi hannayenta da kallo wanda suka sha lalle ba laifi mai kyau, amma da ganin gyalenta da kayan jikinta kasan ba shirin k'warai tayi ba ko aka mata, duk da bata yanayin farin ciki hannu tasa ta janyo mayafin tana fad'in "Haba aunty Zeituna mu ga kwalliyar mana, mu fa ba bak'in ki bane." Kallon juna sukayi yayin da Umaimah har saida tayi dariya saboda ganin kwalliyar dake fuskarta, da sauri ta rufe bakinta tana kallon jagirar da ke fuskar Zeituna wacce ta mik'e zat babu lank'wasa,cike da mamaki Amna tace "Aunty Zeituna, waya miki wannan kwalliyar haka?" Da sauri Zeituna ta d'ago kai ta kalleta sai kuma ta sauke kanta tana mamakin yanda duk suke kiranta da aunty, Umaimah ce tace "Aunty Zeituna, gaskiya tashi ki sake wanka ki zo ki sake shiri, dan kawuna ba zai so ganinki haka ba a darenku na farko." Tintsirewa sukayi da dariya sai Hamna kawai data girgiza kai tana murmushi, ganin bata da niyyar tashi yasa Amna mik'ewa ta kamata suka nufi ban d'aki tana fad'in "Mik'e mana auntynmu, wannan kwalliya taki ai ta asalin 'yan k'auye ce aka miki." Turata tayi ban d'akin tace tayi wanka ta fito dan ta goge wannan kwalliyar marar kan gado, Jamila ce ta mik'e tace ma Hamna "Sis ki duba mata kayan daya dace ta saka yanzu, dan ke ce ke shirin zama gwanar kwalliya da iya tsara kaya." Hararanta tayi tace "Wai ku ina ruwanku da shirinta? Haka kawai ku mata katsalandan, kunsan tana so ko bata so da zaku mata shishigi? Watak'ila fa haka ta iya kwalliyarta, kenan zamu zauna kullum muna yi mata ne?" Amna ce tace "Ke dai babu ruwanki kawai ki mata, in kuma ba zaki mata ba ki fad'a ni saina mata." Hararan Amna tayi tace "Bansan iskanci Amna, ina wasa dake ne? To ba zanyi ba ki mata ke." Mik'ewa tayi zata bar d'akin Amna ta tab'e baki tace "Kar Allah yasa kiyi d'in kiga idan za'a kasa yi mata ne." Duk da Hamna taji zafin maganar amma banza ta mata dan bata son hayaniya, saida ta kai k'ofa zata fita Amna ta sake cewa "Dama tun jiya kike bak'in rai kamar wacce aka aikowa sak'on mutuwa." Juyowa tayi ta kalleta cikin hassala tace "Amna bana son iya shege fa, wallahi karki sake min magana, inba haka ba kuma..." K'wafa tayi ta sake juyawa zata fita Amna tace "Inba haka ba sai me? Me zakayi?" Juyowa tayi ta dawo cikin harzuk'a tana fad'in "Dan Allah in kin cika 'yar halak ki sake tanka min, Amna ki min magana kiga yanda zan kifar dake a wurin nan." *'Yan biyu akwai rigima🤔, ko kuma dai na familyn Gaga ne haka.* Ba tare da wata shakka ba ta matsa kusa da ita tsabar jin masifa tace "Anyi d'in naga me zaki..." Marin da Hamna ta sauke mata a kumatu yasa ta yin shiru bata shirya ba, dafe kunci tayi ta d'ago daga sunkuyawar da tayi bata shirya ba, da tsantsar mamaki ta kalleta tace "Hamna ni kika mara?" "An mareki Amna me zakiyi?" Cewar Hamna a hassale, d'orawa tayi da "Ko zaki rama ne marar kunya?" Ai kuwa Hamna na gama fad'a Amna ta d'auke ta da mari ita ma kamar wasa, jin zafin marin yasa Hamna idonta kad'awa sukayi ja sosai, takaici ne ya lullub'e ta wai k'anwar ta ce ta mareta a fuska, lallai akwai raini tsakaninsu kuma babba, tana shirin kai mata duka Jamila tayi saurin shiga tsakaninsu ta ture Amna gefe guda tana fad'in "Dan Allah kuyi hak'uri ya isa haka, ku bari." Umaimah ma tasowa tayi ta rik'e Hamna ta fara bata hak'uri, wannan hayaniyar ce ta fito da Zeituna daga ban d'aki da kuma Ummy da su Zeinabu dake d'akin Ummyn wanda yafi kusa dana Zeituna, suna zuwa suma rabasu suka fara yi suna bawa Hamna hak'uri wacce ta d'auki zafi sosai, tabbas kowa yasan ranta ya b'ace saboda yanda ta rikid'e ta zama kamar Amna idan tayi zuciya, kuka Hamna keyi tana fad'in "Wallahi Ummy saina tozarta yarinyar nan, dan na sakar mata fuska shiyasa har zata iya d'aga hannu ta mareni, Allah saina ci uwarta a gidan nan dan ta gane da banbanci ni da ita." Ummy ce ke fad'in "Kiyi hak'uri nace ko Hamna ta, ki k'yaleta tunda ke ce babba, muje d'akina ki huta kinji ko." Cikin wani irin kuka kamar wacce aka wa mutuwa tace "Babu inda zanje, Allah saina tattaka ta Ummy, idan ba haka ba kuma kowa zai shiga matsala a gidan nan." Murmushi Ummy tayi saboda ita dai tasan yan biyunta basu da k'ohi yanzu, dan haka ta jata tana fad'in "Naji to muje dai." Tirjewa tayi sosai tace babu inda zata je saidai a barta da Amna, ita ma kuma Amna da su Zeinabu ke rik'e da ita cewa take "Dan Allah Ummy ki saketa ta zo ta kashe ni in zata iya, an fad'a miki tsoronki nake ne." Ganin abun ya k'i kwantawa yasa Ummy daka tsawa tace "Ke Jamila, tunda ba zasu hak'ura ba ku kira Hajia ta zo ta rabasu, ni kam na gaji da wannan jininin kamar kukan tsohuwa." Juyawa Jamila tayi da sauri ta fita daga d'akin, amma zuciyar kowa a wuya take babu wacce tayi yunk'urin dakatawa sai aikawa juna ashar suke da son a sakesu. Jamila na zuwa a falo ta samu Hajia da sauran aminanta da suka rage, saida taje kusa da ita sosai ta sunkuya ta dafa kujerar da take zaune akai cikin k'asa da murya tace "Hajia, wai Ummy tace na fad'a miki ki zo ki ma su Hamna magana fad'a suke, kuma sun rabasu sun k'i su rabu." Wani mugun kallo ta watso mata kamar ta kashe ta da mari tare da d'aga murya tace "Dallah malama b'ace min da gani daga nan, ku mahaukatan ina ne da baku san ta kamata ba? Ina cikin mutane ne zaki zo min da wata maganar banza, to kije ki fad'a musu nace su barsu su kashe kawunansu, tunda su 'yan iska ne ba za'a fad'a musu suji ba." Jiki a sanyaye ciki da haushi Jamila ta juya zata koma, muryar Hajia ce ta tsinta tace "Tunda sun k'i rabuwa cikin lalama kije ki kira min Ammar, shi zai ci uwar kowace sai su zauna lafiya ai." Juyowa Jamila tayi ta kalleta, Ammar kuma? Shine abinda ta maimaita, tasan in dai ya zo to fa sai sunji jiki dukansu, to amma ya zatayi? Wucewa tayi sumi sumi ta nufi b'angaren samarin, tana daf da kaiwa ta had'u da shi ya fito da alama fita zaiyi, saida gabanta ya fad'i ita kam dan sam bata san shiga shirginshi, saida ta d'auke kallonta daga kanshi kafin tace "Yah Ammar dama Hajia ce tace wai ka zo?" Wani farrr yayi da idonshi ya kalli wata bishiyar mai kyau ya dafe k'ugu yace "Ebola, me kuma ya faru yanzun?" Shiru Jamila tayi bata ko kalleshi ba hakan yasa ya daka mata tsawa yace "Da wani bakinki kamar na jab'a, ba dake nake ba kika min shiru? Da gulma ce da kin fad'a ko?" D'agowa tayi kamar zatayi kuka tace "Nima ban sani ba yah Ammar, su Hamna ne ke fad'a a ciki, kuma su Ummy sun rabasu sun k'i su rabu, shine Hajia tace na kiraka ka rabasu." "Wato ni d'an iska ko? Ni ne zan iya rabasu kenan? Ai dama ance kowane kare ma da ranarshi." Jamila dai satar kallonshi tayi ta juya ta barshi, take ya canza tafiyarshi zuwa ta k'akk'arfan soja mai ji da izza ya tunkari b'angaren, fuskarshi kad'ai zaka kalla ta baka tsoro ta saka fargaba da fitsari a wando, dan alamu ne na babu wasa a tare da shi, da haka ya shiga ko kallon Hajia baiyi ba ya nufi d'akin Zeituna da yake jin hayaniyar kuma ya ga Jamila ta shiga can. *Nagode da addua'r ku mutane na, na haihu lafiya haka ma ina cikin k'oshin lafiya ni da beby Khalid, Allah ya bar k'auna masoyana.* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _28_ Yana shiga d'akin babu sallama fuska a had'e ya soma kallon Hamna da Amna, Ummy na ganinshi had'e rai tayi ita ma ta kama hannun Hamna da nufin su fita, durk'ushewa tayi cikin wani irin kuka tana fad'in "Wallahi Ummy saina daki yarinyar nan, kawai ki tafi ki barni da ita." Sake sunkuyawa tayi zata kama hannunta tana hararan Ammar dake tsaye yana kallonta tace "Tashi muje nace Hamna, bana son taurin kai fa." Kamar ba da ita ake magana ba saboda yanda tayi bata ji ba, a hankali ya fara zago belt d'in shi daga jikin wandonshi cikin motsa labb'a a hankali yace "Ku fita ku barni dasu kamar yanda suke buk'ata, tunda 'yan daba ne su." Kallonshi Ummy tayi tace "Kaga malam babu ruwanka, karka kuskura ka tab'a min yara wallahi, inba haka ba kuma ranka zai mugun b'aci." Kallon Jamila tayi tace "Ke wa yace ki kira shi? Ba Hajia nace ki kira min ba?" Cikin turo baki tace "Wallahi aunty na fad'awa..." Shiru tayi saboda kallon da Ammar ya mata, mayar da kallonshi yayi kan Amna wacce ke tsakiyar Zeituna da Zeinabu, cikin dakakkiyar murya yace "Meya had'a ki da ita?" Duk bala'in zuciyarta da masifar dake ciciyarta saita samu kanta da jin fad'uwar gaba, hawaye taji suna neman cika mata ido yayin da jikinta ya fara d'aukar rawa, tafin hannunta tasa ta share 'yar kwallar ba tare da tace komai ba, zaro manyan idonshi yayi masu surkin launin ja ya daka mata tsawa yana fad'in "Tambayarki nake meya had'a ki da ita?" Rintse ido tayi sosai dan mummunar fad'uwar da gabanta yayi, dunk'ule hannunta na hagu tayi ta bud'e idonta, hawayen da take so rik'ewa ne suka zubo, cikin rawar murya tace "Kawai daga zamu sakewa aunty Zeituna kwalliya ne fa, shine tace ita ba zatayi ba nace mu zamuyi, kawai shine tace idan ban daina shiga harkarta ba zata kifar dani, daga 'yar k'aramar magana kawai saita mareni, shine ni kuma..." Shiru tayi ta kasa k'arasawa dan tasan babu abinda zai hanashi gaura mata mari, cikin yanayin muryarshi mai firgita tunani yace "Shine ke kuma me? Kina nufin kice kika rama?" A hankali ta d'an ja baya tana k'yak'yabta ido da turo baki irin eh nima ramawa nayi, ba tare daya kula dasu Zeinabu ba yasa hannu ya jawo hannunta ya direta gabanshi, kallon Ummy take tana so ta bashi hak'uri kar ya daketa, cikin tsawa yace "Kalleni nan." Matsakaitan idonta ta zuba cikin nashi, amma ina tsabar kwarjininshi da tsoronshi yasa tayi saurin sunkuyar da kanta k'asa hawaye na zubowa, sake daka mata tsawa yayi yace "Kalleni ido cikin ido, inba haka ba zan gurguntar dake a wurin nan wallahi, kin dai ji na rantse miki." Kallonshi tayi cikin idon amma hawayen dake ambaliya sun kasa barinta ta fahimci asalin mugun kallon da yake mata, cikin saisaita murya yaja kunnenta sosai yace "Amna wannan sa'arki ce? Tsararki ce ita? Shin ba tana gaba dake ba?" Bayan hannu tasa tana shan majinar wahala ba tace komai ba, sake murd'e kunnenta yayi yana fad'in "Bani amsa mana ina jinki." Rintse ido ta sake yi saboda yanda taji har fitsari na k'ok'arin taho mata bata shirya ba, girgiza kai tayi hakan yasa yace mata "K'adangaruwa ce ta haifeki da zaki dinga juya min kai?" Cikin masifar jin zafin murd'e mata kunne ta sake girgizawa da k'arfin ta tana fad'in "A'a, a'a nace, dan Allah kayi hak'uri yah Ammar." Turata yayi gaban Hamna yana fad'in "Maza to bata hak'uri kafin ranki ya b'ace." Juyowa tayi ta kalleshi alamar bata gane ba, belt d'in hannunshi ya gyara yana fad'in "Ko ba zaki bata hak'urin ba ne kike kallona haka?" Zeinabu ce tace "Ke Amna bansan taurin kai, ki ba yar uwarki hak'uri komai ya wuce." Ummy ce tayi saurin cewa "Bata hak'uri kinji, shiyasa tun farko na so ku sulhunta kanku kafin kuji ba dad'i." Yanda ta had'e fuskarta zai nuna maka tabbas zata bayar da hak'urin ne dan anfi k'arfin ta, amma ba dan haka ba ba zata bayar ba, wata harara ta gallawa Hamna da har yanzu ke durk'ushe tace "Kiyi hak'uri." Tana fad'a ta juya da gudu ta bar d'akin ranta b'ace, cikin takon izza ya dawo gaban Hamna yana kallonta yace "Ke kuma malama kada ki sake saurin d'aga hannunki kika dakar min amarya dan ba jaka bace, bare har ki mareta a fuska wajen da yafi komai daraja, ko ni dole zan koyawa kaina yanda zan dinga tausar kaina ba tare dana mareta a fuska ba saboda tsaro, sannan 'yer uwarki ce ita kamata yayi ku zama kamar aminan juna." Tunda yace amaryarshi Hamna ta d'ago kai da sauri, haka kawai taji kalmar ta daki zuciyarta sosai, sam bata ji dad'in maganar daya fad'a ba, mik'ewa tayi da niyyar zazzaga masa masifa, dan dama saurin hushin nata ya samo asali ne daga abinda ya mata, shiyasa har ta biyewa yar uwarta sukayi cacar baki, sai dai yana ganin ta mik'e ya juya ya bar d'akin da sauri yana mayar da belt d'in shi, ita ma bayanshi ta bi ta fita daga d'akin haka ma su Jamila da Umaimah, Zeituna kad'ai aka bari tsaye jikinta yayi sanyi ta rasa akan me zatayi tunani, a hankali taja k'afa ta koma ban d'akin ta cire katan jikinta ta shiga wanka, sosai ta jima tana goga sabulu mai dad'in k'amshi wanda taga har wata madara-madara ke fita tsabar kyawun sabulun (Dove kenan), tana idawa sabon maclean da brush data gani ta d'auka ta tsabtace hak'oranta kafin ta fito, mai ta shafa ta shafe jikinta da humra data gani a gaban madubinta sannan ta samu turare ta feshe jikinta, babu abinda ta shafa bayan wannan sai nufa da tayi wajen kaya ta fara dubawa, dama dai lefen da aka mata gaba d'aya guda bakwai ne aka d'inka mata wanda zata fara sakawa, kuma kaf d'inki babu mai kyawun wanda su Umaimah suka dare, dan haka kawai ka d'auki doguwar bak'ar riga ta saka wacce ke cikin lefenta mai kyau ta saka, ita kanta data tsaya gaban madubi sai taga ta canza, duk da babu kwalliya a fuskarta, amma ta haska tayi kyau komai nata ya fito, hatta hasken fatarta ya k'ara fitowa, kallabin kayan ta d'ora ta k'ara fesa turare sannan ta zauna kan gadon tana k'arewa d'akin kallo. *Bayan wasu awanni* gidan yayi shiru sosai alamar kowa ya kwanta huta gajiya, lieutenant ne da kanshi ya shigo gidan, Alhaji na zaune a farfajiyar gidan, ledar dake hannunshi ya d'an b'oye bayanshi ya durk'usa yace "Alhaji barka da hutawa." Cike da dattijantaka ya amsa da "Barka Babba, anshigo?" "Eh Alhaji." Ya amsa kanshi k'asa, jinjina kai yayi yace "To ya hidima?" "Alhamdulillah, ya gajiyarku?" Amsawa yayi da "Angode Allah." Cikin girmamawa ya amsa da "Allah ya k'ara girma." Mik'ewa yayi yana fad'in "Ni zan shiga ciki Alhaji, saida safenku." "Allah ya tashe mu lafiya, Saida safe." Nufa babban falon yayi yaji ta bayanshi ance "Alhaji barka da dare." Tsayawa yayi ya juyo danya fahimci muryar wanene, saida ya k'araso wurin da alama shima shigowarshi kenan, hannu ya mik'awa Alhaji yana fad'in "Mai gida ga hajjaju kenan, ana shan iska." Murmushi Alhaji yayi yace "Mijin Amna, ya kake?" Cike da shak'iyanci yace "To gani dai, na gama komai, yanzu Hajiar nake sauraro naji lokacin data d'ibar mana da zata sa mu angonce." Lieutenant dai tsaki yaja ya juya zai wucewarshi Ammar yace "Abba ya na ganka kai kad'ai zaka shiga wajen amarya?" Juyowa lieutenant yayi rai a b'ace yace "Ban gane ba? Ni da ubanwa kake son gani na to?" Saida ya kama hantsar wandonshi irin na yan gayu yace "Eh to, naga kai ka kad'ai ne babu abokin rakiya, ko kana nufin kai kad'ai zaka siyi bakin amaryar?" A hassale lieutenant yace "Eh d'in, ni kad'ai zan shiga, kana da matsala da hakan ne?" "Ah sosai ma." Ya fad'a yana matsowa kusanshi, hannu yasa ya karb'i ledar hannun lieutenant ya juya ya kalli Alhaji yace "Alhaji domin Allah kana ganin ya dace ace ya je wurin yarinyar nan shi kad'ai? Ka fad'a mishi ya nemi d'an rakiya mana." Cikin dariya Alhaji yace "To banda abunka Ammaru yanzu waye zai fito daga gidanshi cikin daren nan? Kuma naga shi ba yaro ba haka ba abokan nashi, kawai ka barshi ya shige." Ba alamar wasa yace "Alhaji ni fa dama ba nufi na kenan ba ya kira wani, masha Allah duk 'ya'yan da Allah ya hore mishi ace mun kasa rakashi saiya kira wani, gani babban d'a, kawai muje na raka ka Alhaji." Ya k'arashe maganar yana kallon lieutenant. Haushi ne yasa lieutenant kai hannu zai fizgo ledarshi yana fad'in "Dan ubanka bani ledata, Allah ya tsareni na rasa wanda zai rakani sai kai." Rik'e ledar yayi shima kuma Ammar ya rik'e sosai ya had'e rai kamar zaiyi fad'a, shima lieutenant fuskarshi a had'e ya kalleshi yace "Zaka sakar min ledar ko saina barar da kai a wurin nan? Ammar bana son iskanci fa, ina wasa da kai ne?" Shima cikin hadd'ad'ar fuskarshi yace " Abba, wallahi tallahi saina raka ka ko baka so, kawai muje." Gyara tsayuwa lieutenant yayi yana kallonshi da mamaki, hannunshi ya kama ya nufi dashi babban falon yana fad'in "Muje haba na sadaka da ita, ina fatan dai ba sai ka tsaya wani ja musu kunne ba? Tunda ai uwarmu ba hayaniya gareta ba, kawai kayi tazarce." Dariyar da Alhaji ya tintsire da ita ne ta dawo da kallon lieutenant kanshi, ba tare daya tsagaita da dariyar ba Alhaji yace "Kawai kuje babba, koba komai shi d'in babban d'an ka ne kamar yanda ya fad'a." Nuna Ammar yayi da yatsa yace "Alhaji da wannan mahaukacin? Haba dai." Sai lokacin ya daina dariyar yace "Kuje kawai ba komai." K'iiiii Ammar yaja hannunshi har cikin falon, bai kuma yi alamar tsayawa ba har suka tunkari d'akin Zeituna, suna kaiwa bakin k'ofar babu wani tsayawa kawai ya kama murfin k'ofar zai bud'a, da sauri lieutenant ya jawoshi baya yana fad'in "Wai kai wane irin mahaukaci ne dan Allah? Haka zaka shigar mata d'aki babu k'wank'wasa k'ofa ko sallama? Kasan a wane yanayi zaka sameta?" Wata shegiyar dariya yayi yace "Ikon Allah, Babanmu tun kafin ka shiga cikin? Ni ko a tunani na dai amarya indai budurwa ce ai yanzu za'a sameta zaune ne akan gado, akan gadon ma a tsakiyarshi." Tsaki lieutenant yayi ya k'wank'wasa k'ofar d'akin yana hararan Ammar dake kallonshi ido cikin ido, murmushin zaka shiga hankalinka Ammar ya mishi sanda ya bud'a d'akin ya shiga, bin bayanshi yayi ba tare da yayi sallama ba kamar wanda baisan mahimmancinta ba. Suna shiga ba b'ata lokaci ya samu kujerardake gaban madubi ya zauna, tsaf ya k'arewa d'akin kallo tare da k'urawa Zeituna ido wacce taja kallabin rigarta ta rufe fuska, ganin kallon da yake mata gashi baida niyyar fita baya so ya mishi b'aram-b'arama yasa yayi gyaran murya, a hankali cike da k'asaita ya juyo ya kalli lieutenant d'in sannan ya kalli Zeituna, ledar dake hannunshi ya aje mata gabanta yace "Amm...Zeituna ko? To ga kazarki." Wani kallo lieutenant ya mishi amma shi ko kulashi baiyi ba sai kallon Zeituna daya sake yi a nutse ya d'an tab'e baki yace "To wai ke da wannan rigar aka kawoki ne? Meyasa baki saka leshe ko chadda ba? Ba'a miki d'inki bane?" Wurk'il wurk'il Zeituna tayi da ido a cikin kallabinta, duk da Ammar ko ma tace mazan gidan ba mazauna gida bane, amma dai tasan Ammar baud'add'en mutum ne, lieutenant kuma kallonshi yayi rai a b'ace yace "Malam nagode da rakiyar da ka min, zaka iya tafiya ko?" Gira ya d'aga tare da jinjina kai ya mik'e tsaye ya kalleta yace "Amaryar Abba, nasan dai kinsan mahaifiyarmu kuma kinsan wacece ita, ina fatan kafin ki shigo gidan nan kin tsarkake zuciyarki, dan akasin haka ba zai mana kyau ba mu duka, domin kuwa mahaifiyata ita ce komai nawa, zan iya yin komai akan ta duk wanda yace zai b'ata mata, fatan za'a kiyaye saimu zauna lafiya." Kallon lieutenant yayi yace "Abba, Allah yasa auren nan daka k'ara ba zai zama silar da za ayi sanadiyar zubar hawayen Ummyna ba, dan gaskiya ba zan juri haka ba, saida safe Abba na." Yana gama fad'a yasa kai ya bar d'akin, lieutenant kam kasa motsawa yayi kafin daga bisani ya kalleta yace "... *Alhamdulillah* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _29_ "Tashi muje wajen uwarsu Ammar ko." Hawayen da take wanda baisan dasu bane ta shiga gogewa, shiru yayi yana kallonta yana mamakinta, jin shiru ita ma yasa ta fara d'aga sautin kukanta saboda ita dai abun ya fara bata tsoro, bata gama gamsuwa da cewa ita matar lieutenant bace aka samu matsala tsakanin Hamna da Amna, yanzu kuma ga kashedin da Ammar ya mata wanda yake d'a ne ga mijinta, ita kam sai yanzu ta fara hangowa kanta uk'ubar data jefa kanta ta yarda da auren Abban Ammar, kamar daga sama lieutenant yace mata "Idan kin gama kukan ki tashi mu tafi to." Cikin rawar jiki Zeituna ta mik'e har ta k'afafun ta na hard'ewa, lura da hakan yasa lieutenant tambayar kanshi "Anya kuwa wannan mu'amular ce ta dace ka mata a matsayinta na yarinya?" Ganin sai sauri take ta fita daga d'akin yasa ya rik'o hannunta ta baya, cak ta tsaya ta juyo da sauri ta kalleshi, suna had'a ido saita sake b'arkewa da kuka ta rufe fuska da hannu d'ayan, a lokacin tausayinta ne yaji ya daki zuciyarshi, tunawa da yayi har yanzu baiji muryarta ta fito fili ba, a hankali ya jawo hannunta ya kwantar da ita kan k'irjinshi, wani lafiyayyan masauki ya mata a cikin jikinshi tare da zagayeta da hannayenshi ya fara daddab'a ta alamar tayi shiru, Zeituna kam take kukanta ya tsaya kamar anyi ruwa an d'auke, shiru tayi yayin da bak'on al'amarin ya nemi zautar da tunaninta, a d'aya b'angare kuma numfashinta ne taji yana kokawar barin gangar jikinta, wannan mafarki mai cike da tarin al'ajabi da rud'u ya addabeta, har yanzu ta kasa tashi daga wannan baccin da ba zata kira shi da mummunan bacci ba, haka kuma ta kasa yin farin ciki ko da a iya mafarkin ne, wani zazzab'i ne taji yana neman rufeta har jikinta ya fara b'ari saboda rashin sabon yanayin data tsinci kanta a ciki. Shi kanshi lieutenant wani bak'on al'amari ne ya ziyarce shi, amma saiya dake ya ci gaba da shafa har yayi k'arfin halin fizgo nutsuwarshi ya d'an sunkuyo yana lek'o fuskarta cikin dakusashiyar murya yace "Kukan ya isa haka, karki damu da halin Ammar, muma kanmu haka muke fama da shi, ya kamata ace kinsan shi bai kamata ya baki wahala ba, kinji ko? Ka da ki sake zubar masa da hawaye, idan ya fahimci haka zaki shiga tara a hannunshi, ba zai duba matsayinki na matar mahaifinshi ba, dan ko uwarshi ce zai iya yi mata haka, karki damu kinji." Har ga Allah Zeituna ba kukan abinda Ammar ya fad'a mata take yi ba, amma jin abinda lieutenant ya fad'a saita tambayi kanta "Meyasa yake tunanin Ammar ne ya sani kuka? Me Ammar yayi da har yayi tunanin maganganunshi ne suka b'ata min rai? Soyayyar mahaifiyarshi ce ya nuna min a fili, hakan kuma ya birge ni sosai, tabbas shi d'in mai k'aunar mahaifiyarsa ne, tunda har kai mahaifinshi ya maka kashedi akanta." A hankali lieutenant ya raba jikinsu tare da nufa k'ofa, hakan kuma shi ya dawo da hankalinta kanshi, a hankali ta bi bayanshi gabanta na fad'uwa na fargaban abinda zata tarar, yana shiga d'akin da sallama ya samu Ummy ta fito daga wanka da doguwar rigar bacci mai laushin gaske ta zallar audiga, kanta babu d'an kwali sai dogon gashinta daya sha kitso yake kwance har gadon bayanta, tana ganinsu tayi saurin juyawa bayanta ta d'auki wata hula ta d'ora akan tana mai fad'ad'a murmushinta tana fad'in "Sannunku da zuwa." Murmushi ya mata yace "Sannu da hutawa uwar 'yan biyu." Kallon Zeituna tayi wacce kanta ke k'asa tana wasa da hannayenta tace "Amarya sannu ko." K'ala ba tace ba haka kuma bata kalleta ba sai ita ta sauko daga kan gadon ta kama hannunta ta juyo ta kalli lieutenant da harya zauna bakin gadon tace "'Yallab'ai ba dai har yanzu baka bar k'anwata ta huta ba?" Murmushi yayi yace "To me tayi da take buk'atar hutun?" Kallon Zeituna tayi tace "Duk da haka dai tana buk'atar ta huta yallab'ai." Da hannu ya mata alama yana fad'in "Zo zauna to magana zamuyi." Matsawa tayi kusanshi amma bata zauna ba tayi murmushi cike da dattako tace "Yallab'ai nasan meya kawoka, dan haka ba sai ka wahalar da kanka ba, Zeituna k'anwata ce kuma abokiyar zama na, insha Allahu zamu zauna lafiya ta yanda zakayi alfahari damu, mun riga da mun fahimci junanmu, tunda ba yau muka san juna da ita ba, nasan wacece Zeituna, duk da ana cewa d'an adam ya kan sauya, amma ina da yak'ini akan Zeituna cewar ba zata canza ba, yarinyar kirki ce ita d'in, tana girmamani da ganin darajata, zanyi k'ok'ari naga na rik'e wannan girman sannan nima na bata matsayinta, insha Allahu na maka alk'awarin ba zaka tab'a samun mu da wata matsala ba, kawai kuje ku kwanta." Cike da jin dad'i da kuma k'aunarta ya sakar mata murmushi yace "Allah ya miki albarka uwarsu Ammar, nagode miki sosai, hak'ik'a samun mace irinki a zamanin nan sai an tona, Allah ya bar min ke." Murmushi tayi kanta k'asa tace "Nagode." Kallon Zeituna yayi dake tsaye kanta k'asa har yanzu yace " Ke me zaki iya cewa to? Kin dai ji abinda yer uwarki ta fad'a." Rau rau ta fara yi da ido ko d'agowa ba tayi ba bare tayi magana, murmushi Ummy tayi tace "Yallab'ai kai bai ma kasan ai ba zatayi magana, kunya take ji har yanzu, amma ka bata d'an lokaci k'ank'ane." Mik'ewa yayi yana fad'in "Shikenan to, saida safe ko." Zeituna na jin haka ta juya da sauri dan barin d'akin, shi kuma ko a jikinshi saida ya jawo kan Ummy ya manna mata sumba a goshi tare da shafar gefen fuskarta kafin ya sake ce mata "Saida safe masoyiyata, ki kular min da kanki." Murmushi kawai ta masa har ya fita, yana fita ta fad'a kan gado ruf da ciki tayi shiru, tabbas ta so tayi kuka, amma kuma cikin ikon Allah saita fi k'arfin zuciyarta har bacci ya d'auke ta. A wajen lieutenant kam shima yasha gwagwarmaya da zuciyarshi, dan so da dama zuciyarshi ce ke tunasar dashi wannan auren fa na mahaifina ne, duk rashin kulawar da zan nuna mata kamar na wofantar da maganar mahaifina ne, da hakane fa har suka kwanta bacci yayi dubarar mayar da ita matarshi ta sunna. *07:05* duk da yau asabar ce amma kowa na gidan ya gama shiryawa, yara sunyi shirin islamiyya manya kuma zasu fita, Hajia na zaune a inda ta saba zama, Zeinabu da Soueiba da Ummy na ci gaba da gyaran gidan tare da Iya, sai su Nana dake ta k'ok'arin kammala abin karin kumallo, colonel ma cikin shirin tafiya ya fito ya gaishe da Hajia, kamar kullum ta amsa babu wani sakin fuska bare sa albarkarta, bai jira komai ba ya d'auki hanya tare da masu tsaron lafiyarsa dake biye da shi. Tun a falonsu suka had'e kowa ya fito daga d'akin shi, hannu Amar ya bashi yana fad'in "Malam Ammar ka tashi lafiya?" Hannu ya mik'a mishi a cikin mak'oshi ya amsa da "Um." Murmushi kawai yayi yace "Tun jiya ina ta nemanka ban ganka ba, ina ka shiga ne haka?" Ba tare daya kalleshi ba yace "Yaushe ka fara aikin jarida?" Wani murmushin ya sake yi yace "Daga tambayar k'waya d'aya? To Allah ya baka hak'uri." Fuska a had'e yace mishi "Idan ya bani kabi dare ka k'wace mana." Girgiza kai kawai Amar yayi yace "Kasan banji dad'in rashin ganinka ko d'aya daga cikin sabgar Abba ba, Ammar meyasa kake haka? Ba kyau fa." A daidai farfajiyar gidan yayi tsaye ya juyo ya kalleshi yace " Dan Allah Amar samu madaki ka bibbige ni, shine kad'ai zaisa nasan baka ji dad'i ba, yau ni naga jaraba, dole ne saina je d'aurin auren? Yanzu da banje ba meya faru? An fasa ne? Ina ce amaryar a gidan nan ta kwana kuma tare dashi." Juyawa yayi a fusace ya tunkari falon Hajia yana fad'in "Kawai mutum ka addabeni ka addabi rayuwata, kuma ni na fad'a maka banje ba? Ina ce ni na rakashi ma d'akin amaryar, haka kawai ka dameni da surutu." Amar na jin abinda ya fad'a ya matso da sauri yace "Me kace? Ka raka shi fa naji ka ce?" Sake tsayawa yayi ya juyo a hassale yace "Eh haka nace, ni na raka shi, da matsala?" Girgiza kai yayi dan ya fahimci yau ya tashi da yan sababin, shine ya fara shiga falon ba sallama kamar kullum inda Amar ke biye dashi da sallama, kujerar dake gefen Hajia ya zauna ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana fad'in "Ina jin dad'in zaman kujerar, bansan meyasa ba bana gajiya da zamanta." Kallon Hajia yayi wacce ita ma ta kafe shi da ido tana kallonshi, murmushin nan dai daya saba mata na iskanci ya mata yace "Au na manta fa, ashe ni d'in jinin Hajia ne, jika na farko ga hajajju mutan makka, dole ne kujerar nan ta dinga burgeni, ashe gado nayi, dan naga kema ke da kujerar nan kamar kujerar mulki ce, duk wanda zai bud'e idonshi a gidan nan to zai wayi gari ne ya ganki a samanta, haka kuma duk wanda zai kwana to zai rufe idonshi ne bayan ya miki gani na k'arshe a kanta." Had'e rai tayi tace "Kai ka kiyaye ni, meya kawoka nan d'akin?" Dariya ya mata yace "Karki damu Hajiata, insha Allahu ko a lahira saikin zauna kan kujerar nan a matsayin shugabar tsofaffi ta gidan aljanna." Hannu ta kai cikin zafin nama zata mareshi, da azama cikin isa da k'asaita ya cabko hannunta ya rik'e sosai, kallon baki da hankali ya mata yasa d'aya hannu yana shafar hannunta yana kallon k'wayar idonta, tana kallonshi ya kai hannun a bakinshi ya sumbaci bayan hannun nata kafin ya kalli hannun yace "Ni kam Hajia in tambayeki mana?" Jin tayi shiru tana kallon sarautar Allah yasa yace "Nasan dai zamanin kina budurwa hannayenki abun sha'awa ne? To amma ya akayi yanzu naga sun zama haka? Duk sunyi tamoji sun jeme sai aukin jijiyoyi kamar..." Fizge hannunta da tayi yasa yayi shiru ya kalleta, hararenshi tayi tace "Allah ya wadaranka Ammar, wallahi ba dan kayi kama da shalele ba da sai nace kai ba jini na bane, amma ba laifinka ban nawa ne." Gyara zama yayi irin ya sa mata bak'in ciki yana fad'in "Da gaske? To amma me yasa kika ce haka? Kina nufin duk ahalin nan naki ni kad'ai ne d'an baiwar da yayi nasarar ya gadoki ta ko wani fanni?" Sakin baki tayi da alamar mamaki a fuskarta, za tayi magana ya sake cewa "Kuma da kika ce muna kama da shalele, shin shine yayi kama dani ko nine nayi kama dashi? Ko kuma dai ke ce mukayi kama dake?" Nuna shi tayi da yatsa tace "Dan ubanka in kana k'aunar uwarka ka tashi ka bar d'akin, wallahi ban son ganinka." Tsaf ya mik'e ya kalleta yace "Idan kika ce ba kya son gani na a cikin gidan nan ma zan iya daina zuwa, amma fa saboda soyayyar uwata, dan ba zai yiwu na bar gidan nan ba bayan kuma nine babban magajin gidan." Wani kallo ta mishi a shek'e tace "Wai kai a ganinka kaine babban magajin gidan nan?" Dariyar rainin hankali ya mata yace "Ba'a ganina bane, a ganin kowa ma hakane, shiyasa fa hausawa suka ce *ko ba'a sonka a haifeka da fari*, gashi dai ni d'in ba sona kuke ba amma kuma ni na fara bultsowa duniyar, kai wallahi ni d'in mai sa'a ne." Hannu ya bawa Hajia da nufin su kashe yana fad'in "Ban biyar Hajia ta, Allah ina mugun sonki." A daidai lokacin da Ummy ta fito daga madafa kenan, yayi daidai da fitowar lieutenant da Zeituna a bayanshi Hajia tace " *Ni kuma na tsaneka Ammar, kaji da kyau, wallahi bana sonka har zuciya ta, bana son mu'amula da kai saboda kamar mahaukaci kake, Ammar ba dan ina asibitin ba a lokacin da uwarka ta haifeka da sai nace kai ba jini bane, wallahi sai nace wani d'an Allah bani ne kai, sakarai kawai.*" Wata marainiyar dariya ya mata tare da k'ok'arin mayar da hawayen da suka cika idonshi taf, gyara tsayuwa yayi ya shirya dan ya fad'a mata abinda har ta mutu bata mantawa, sai dai kuma kafin ya fad'a Hajia ta juyo ta kalli Ummy tace "Sa'ada kina jin rashin mutumcin da d'an ki ke shuka min ko? Wallahi idan bai kiyayeni ya kusa barin gidan nan." Daga inda take tsaye ta wurgo masa da harara kafin ta kalli Hajia tace "Kiyi hak'uri Hajia, ni kaina al'amarin shi ya fara bani tsoro, hakan yasa ma nake ganin da k'yar in aljanu basu shafe shi ba, dan a yanzun ni kaina barinshi gidan nan ne kad'ai kwanciyar hankali na." Wani shak'iyin murmushi Hajia tayi ta kalleshi tace "Kaji ko? Uwarka ma data haifeka tana so kayi nesa da ita, bare kuma ni da ban haifeka ba, dan haka ka kiyaye." Tunda Ummy ta fara magana Zeituna dake nesa da ita ta k'ura mata ido, jin furucinta akan Ammar ba sabon abu bane a wurinta, amma ta rasa dalilin da yasa yau taji babu dad'i, a zuciyarta take fad'an "Akan me Ummy zata fad'i haka akan d'an data haifa? Meye ga Ammar d'in da har ya dace da wannan furucin?" Ita kam bata gani ba sai ma zunzurutun soyayyarta da yake d'awainiya da ita, soyayyar da har ta isa ta sashi ya ma mahaifinshi kashedi akan ta, amma ace ita tana fad'in haka akan shi, gaskiya har ranta ba taji dad'i ba. Lieutenant kam kallonta yayi kawai ya tako ya zo gaban Hajia ya gaisheta, duk lokacin Ammar na tsaye da Amar a bayanshi, kawar da kanshi gefe yayi ya d'anyi murmushi mai nuna k'unar zuciya da takaici, lokaci d'aya kuma ya kalli Ummy yana wannan murmushin yace "Ina da shafar aljanu kam, na tuna muku idan kun manta, mufa duk aljanunmu na gado ne, sai dai bansan daga ina ne muka gadosu ba, daga b'angaren uwa ne ko kuma uba, ni kuma aljanin daya shafeni sunanshi *ifritu*, shiyasa muke kama da shi a halayya." Juyawa yayi ya bar falon lieutenant ya bishi da kallon jin haushi, sai lokacin Zeituna ta tako cikin mutuwar jiki dan dama ga ciwon jikin da ubansu Ammar ya saka mata, ga kuma al'amarin wannan gidan data gama fahimta ba'a zaman lafiya, tana zuwa kusan Hajia ta zube gwiwoyinta k'asa ba tare data had'a ido da ita ba tace "Ina kwana Hajia." Wani banzan kallo Hajia ta mata ta yamutsa fuska tace "Mik'e." Jiki na rawa Zeituna ta mik'e tsaye kamar yanda Hajia tace, sake kafeta tayi da ido tace "Wuce ki zauna." Ta fad'a tana nuna mata kujerar dake fuskantarta, rintse ido tayi ta fara takawa da k'yar har ta isa kujerar ta zauna, tana zaman ta d'an gyara zamanta kamar zata zame daga kan kujerar saboda rad'ad'in da take ji, tab'e baki Hajia tayi ta kalli lieutenant tace "Hassan dan Allah ko kunya baka ji ba? Yanzu k'azamar yarinyar nan ce daga kawota jiya shine har ka kusanceta, ashe dama kai ma kana sonta munafurcine kawai irin naku na maza." Ummy na jin haka ta bar wurin tayi madafa kamar zatayi kuka, tunda ya rintse ido bai bud'e ba sai sanda kanshi da yayi k'asa ya kasa ko da motsin arzik'i, hararenshi tayi tace "Tashi dallah malam ka tafi inda zaka, ko kuma ba zaka fita ba yau zaka zauna wajen yar tsanar taka ne?" Sululu ya mik'e ya nufi k'ofa bai yarda ya had'a ido da kowa ba, yana daf da isa bakin k'ofa tace "Sakarai kawai, wannan ma har mace ce." Saida ya shiga mota ya zauna ya waro idonshi da kyau, take a wurin yaji wata siririyar k'walla ta gangaro mishi a gefen idonshi, yatsa yasa ya share kafin ya tayar da motar ya bar gidan. Ammar ma na fitowa daga nan d'akinshi ya koma ya kwanta zuciyarshi babu dad'i. Haka ma Zeituna daga nan wurin kasa tashi tayi saida Hajia ta kalleta cike da k'yama tace "Kinga yarinya, kada kiga anyi auren nan har d'ana ya sanki 'ya mace ki d'auka wai kin samu wurin zama kenan, ba zaki tab'a jin dad'in zaman nan ba indai ina raye, nafi kowa saninku ku talakawan nan, na tabbatar akwai abinda kika wa Alhaji da yasa ya aura sa d'an shi ke, watak'ila ma shi Alhajin kika so samu." Da sauri Zeituna ta d'ago kanta ta kalleta, amma kwarjininta yasa ta kuma sadda kanta k'asa, ci gaba tayi da cewa "Amma da kika ga babu wuri a gidan da zaisa ki samu sunan kishiyata shiyasa kika samu babban d'an mu, to duk da haka baki tsira daga kaidi na ba, dan nasan kinsan ni ke mulki a gidan *Suley Gaga*, abinda na fad'a dashi ake aiki ko ba'a so, ba wai 'ya'yana ba, har shi kanshi mijin nawa da kuma jikoki na ni ke juya al'amuransu, dan haka ki kiyayeni wallahi." Saida ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya ta nuna mata k'ofar madafa tace "Malama tashi ki shiga sahun masu aiki, karki d'auka kinyi aure a cikin gidan nan ne dan ki samu hutu daga waccen bautar da kike, ina! Ba haka bane? Yanzu ma bauta ta fara, dan zaki min kuma ki ma mijinki da 'ya'yan danginshi, dan haka tashi ki fara tun yanzu dan ba hutu ya kawoki ba." Ai da sauri Zeituna ta mik'e ta nufi madafar ta ma manta da ciwon dake jikinta, tana shiga dukansu suka juyo kallonta, Zeinabu kallonta take tana murmushin mugunta wai an ma Sa'ada kishiya, cike da izgilanci tace "Lah! Amarya, meya kawoki madafa yanzu? Dan Allah ki koma karki ja mana magana, mu ma ba girki mukeyi ba kawai dai muna taya su Nana ne." Cikin rashin sakin jiki Zeituna tace "Ina kwananku aunty." Soueiba ce ta amsa mata da "Lafiya lau Zeituna, antashi lafiya?" A hankali ta amsa da "Lafiya lau." Soueiba ce ta sake cewa "Ya kwanan bak'unta kuma?" Shiru tayi wannan karan sai Sa'ada da tace "Kije ki zauna zamu k'arasa." Zatayi magana suka ji muryar Hajia a bayansu tace "Duk wannan yawon naku amma girki ya kasa kammala sama da awa d'aya?" Kowa a tsorace ya juyo uwa uba Zeituna da taji kamar tayi fitsari, cikin i'ina Nana tace "Kiyi hak'uri Hajia, saura kad'an ya k'arasa nuna ne." Zeinabu ma wurk'il wurk'il tayi da ido tace "Bari naje ni na gyara wurin cin abincin kafin ku ida" Fita tayi Hajia ta bita da harara kafin ta kalli Nana tace "Na baki minti biyar naga komai a gabana, idan ba haka ba kin dai san akwai masu neman aiki dake jiran samun irin damarki." Tana fad'a ta juya ta fita, da sauri Nana ta sake bud'a tukunyar dan duba perper soup d'in kayan cikin ragon, amma abun mamaki da al'ajabi yana nan kamar dai yanda ta sakashi, a hakan ma wai dan ta silalasu tun jiya ta aje, amma yanzu kama daga kayan miyan zuwa naman komai na nan da ranshi yanda ta zuba, idonta cike da hawaye ta kalli Ummy tace "Aunty, wallahi har yanzu ko alamar dahuwa baiyi ba, bansan ya zanyi ba, gashi Hajia ta bani k'ank'anin lokaci, nasan lokacin barina gidan nan ne yayi." Soueiba da ummy6ne suka matsa suka duba tukunyar, da tsantsar mamaki Soueiba tace "Amma ya ci ace abun nan ya dahu duba da ko da na sameki madafar nan har kin soya miyarki." Ummy ce tace "Gaskiya kam, dan ko ni da na zo daga baya na samu tana shirin tsayar da ruwan miyar, da shigowata kuma yanzu a k'alla na d'auki minti kusan talatin, amma ace bai dahu ba? Abun kam da mamaki." "Yanzu ya zamuyi? Wallahi a tsorace nake, Hajia ta turo ni ne dan na kama aiki, kar ta d'ora min laifin." Cewar Zeituna a matuk'ar razane. Matsawa Ummy tayi ta sake bud'ewa tukunyar wuta tana motsawa ta ga ko ya fara d'aukar hanyar dahuwa, babu wannan alama dan haka ta rufe tukunyar tace "Mu bashi minti biyar d'in shima muga ko zaiyi." Baya suka ja wasu daga ciki suka zauna kan kujerun da suka k'awata madafar suka buga tagumi, dan kowa yana da tabbacin ba zai sha ba inhar basu gama kan lokacin da aka basu ba. Lokacin da aka basu na cika Ummy tayi saurin bud'a tukunyar, amma juya iya yau babu abinda ya sauya, abun mamaki ne wannan matuk'a, dukansu babu wacce bata nuna alamar wannan mamakin ba, Ummy ce tace "Anya kuwa? Ko dai..." Sai kuma tayi shiru sai Soueiba ce tace " 'Yan biyu?" Ba tare data kalleta ba tace "Bani da tabbas, amma kuma ai basu da k'ohi yanzu." "Kada muyi saurin yanke hukunci, amma wannan abunda yake faruwa yafi kama da aikin 'yan biyun gidan nan." Cewar Soueiba, girgiza kai Ummy tayi tace "Ko hakane ma sai dai aikin Amna, dan tafi 'yer uwarta mugunta tun suna yara haka nasha wahalarsu." Ajiyar zuciya Soueiba ta sauke tace "Sai kiji ki lallab'a mana ita mu samu mu ida girkin nan." Murmushi Ummy tayi tace "In dai har Amna ce, to ba zata hak'ura ba sai dai kawai wanda ya rabasu jiya yanzun ma ya bata hak'urin, dan nasan tana fushi ne saboda an kirashi ya tilasta ta ko kuma dai dan tabawa yar uwarta hak'uri." Soueiba ce tace "To kiyi magana da Ammar d'in mana shi ya rarrasar mana ita." "Ba zan iya ba, ke kije." Ta fad'a kai tsaye. Kallonta Zeituna tayi sai Soueiba data kalli Nana tace "Kinga Nana, tun kafin Hajia ta dawo ki hanzarta b'angarensu Ammar ki kira shi, dan naga motar shi har yanzu tana nan alamar bai fita ba." "To." Nana ta fad'a tana fita daga madafar, a hankali ta bi ta bayan Hajia ta sulale ta bar d'akin ta je b'angarensu Ammar, babu kowa a falon amma kuma k'ofar bud'e, ita kuma har ga Allah tana shakka da tsoron halin Ammar data shiga dan ta bubbuga k'ofar shi, dan haka ta juyo ta zab'i ta gaya musu su suje da kansu, tana dawowa kuma Ammar ya d'auki makullan mota ya bar gidan wanda yayi daidai da fitowar Soueiba dan ta mishi magana, amma kash har ya fita daga gidan sai komawa tayi. Sanda Hajia taji meke faruwa da kanta ta samu Amna har d'aki tana gaggawar shiryawa zata tafi makaranta wajen jarabawa, tatas ta mata ta zageta uwa da uba sannan tace in har abincinta bi dahu ba zata kuma ci mata uwa, haka Amna ta fita rai a b'ace akan motonta dan Hamna ta jima da tafiya, amma tayi niyyar yau Hajia ba zata ci abincin ba ko da na rana ma tunda bata iya bayar da hak'uri ba. A tak'aice dai 😂 Hajajju sai yan dubaru tayi, yara ma haka aka musu dubaru aka tura su makaranta, Ummy ma haka dubarar tayi kafin ta wuce asibiti inda ta samu Ammar yau ya rigata zuwa, amarya Zeituna ma a d'akinta ta samu madara da cornflakes ta mishi had'in kauri tasha ta kwanta tana tunanin ahalin gaga. Da rana sam Nana ba tayi tunanin komai ba ta gyara shinkafa ta bayar aka b'arzota ta d'ora tukunyar dambu, ba b'ata lokaci tukunya ta taso aka fara yamutsa dambu, ana gama gyara komai aka d'ora a madambaci aka rufe, nan Nana ta shiga sarrafa mahad'in dambu, 'yar k'aramar sauce ce mai nik'akk'en nama da albassa mai yawa, saida ta fuskanci yanzu dambunta ya isa ta dubashi ta tunkari tukunyar, tana bud'awa bud'e baki tayi kamar zata k'urma ihu tare da d'ora hannu d'aya bisa kai tace "Na shiga uku, yanzun ma?" Da sauri Zeinabu data shigo tace "... *Alhamdulillah*😍 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _30_ "Mun shiga uku! Kar dai ki ce har yanzu ma ba zamu ci abinci ba?" Cike da tabbatarwa tace "Ai kuwa dai wallahi da alama." Juyawa tayi ta fita tana fad'in "A'a wallahi ba zai yiwu ba, bari na d'auko wayata na kira Sa'ada ta zo ta sa Amna ta sakar mana tukunya, yau ni naga ikon Allah." Tana daf da kaiwa d'akinta lieutenant ya shigo, wanda ya kasa zama ya matsu ya ga halin da Zeituna take ciki, sunkuyar da kai tayi tace "Ina wuni Abban Ammar." Cikin sakin fuska ya amsa da "Lafiya lau, ya gidan?" Ba b'ata lokaci tace "To da sauk'i dai gaskiya." Da mamaki ya kalleta yace "Lafiya dai ko? Ko wani abun ya faru ne?" Cikin sunkuyar da kai ta fad'a mishi duk abinda ke faruwa, murmushi taga yayi yace "To ku samu ku lallab'a ta mana, kunsan dai fad'a da zagi ba zaisa ta huce ba." "Eh hakane, yanzu ma zan d'auko waya ne na kira Sa'ada saita lallasar mana ita." Da 'yar dariya lieutenant yace "To ke ba zaki lallab'ata ba?" "To ai ni bansan ta inda zan fara bane, ita kuma ta saba da rigimar bibbiyu dama." Dariya ya sake yi yace "Da gaskiyarki kuma, tana ina Amnar?" Nuna sama tayi tace "Tana sama dai a tunani na." "Bari na jaraba na gani ko zan iya." Ya fad'a yana wucewa d'akinsu dake sama, zaune tayi falo ta jira shi ya fito taji ya suka k'are, yana zuwa saida ya k'wank'wasa k'ofar d'akin yayi sallama, kusan a tare Hamna da Amna suka amsa wanda kowace ke kan gadonta babu mai kallon wata, saida kowace ta gyara zaman tufafinta kafin Amna da gadonta ne farko ta taso ta bud'e k'ofar, gaishe shi tayi ya amsa cikin sakin fuska tare da dafa kanta, murmushi yayi kafin yace "Amnata baki jin yunwa ne?" Da sauri ta d'aga matsakaitan idonta ta kalleshi sai kuma tayi k'asa da su tana jujjuyasu, jin shiru yasa yace " 'Yata, yunwa nake ji, kuma na zo gida an fad'a min wai kin rik'e tukunyar girkin, shine nace bara na zo na rok'i alfarma, ko baki saketa dan ni ba ki saki dan k'annanki da kuma angonki Alhaji, wanda kinsan basa juriyar yunwa, da safe ma ance basu ci wani abun kirki ba." Ganin tayi shiru yasa ya sake dafa kanta yace "A taimaka mana kinji, kiyi hak'uri komai ya wuce." D'agowa tayi ta kalleshi tayi murmushi tace "Ba komai Abbanmu, nima ba'a son raina bane haka ta faru." Murmushi ya mata yace "Nagode 'yata, Allah miki albarka." Da murmushi ta masa da "Ameen Abbanmu." Juyawa yayi ya samu Zeinabu zaune yace "To ku tashi ku duba tukunyar ku gani." Yanda yayi maganar yasa ita ma tayi dariya tace "Yaran nan, mun gode Allah da yasa basu da k'ohi, da ina ga zuwa yanzu duk mun kamu da ciwon yunwa." Dariya yayi yace "To wai ya akayi ma haka ta faru bayan kuma basu da k'ohi? Abun da mamaki fa." "Wallahi nima ya ban mamaki." Madafa ta wuce shima ya shige d'akin Zeituna, kwance ya sameta akan sallaya ta idar da sallah, yanzu ma doguwar riga ce jikinta da hijab, sululu ta mik'e zaune cike da kunya tace "Sannu da zuwa, ina wuni." Yaji dad'in gaisuwar data mishi dan haka ma ya saki murmushi ya sunkuya ya d'agota ta mik'e tsaye, saida suka k'arasa bakin gado ya zauna sannan ya zaunar da ita kan cinyarshi yana kallon fuskarta, yanda take sunkuyar da kai kamar zata nitse k'asa, d'ago hab'arta yayi ya juyo da kallonta kanshi yace "Wai ke yaushe kunyar nan zata k'are ne? Ba zan iya tuna ranar da muka had'a ido dake ba fa? Ya kamata ace ance yanzu kin saba ko dan igiyar data d'aure mu wuri guda ni dake." Zeituna dai k'ala ba tace ba sai sunkuyar da kai da take, ba tare daya daina mata kallon nan ba yace " Na zo duba jikinki ne fa, to ya kike ji yanzu? Ba kya jin ciwon komai?" Da sauri tasa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta saboda tsananin kunyar data kamata, dariya yayi tare da k'amk'ame ta sosai a jikinshi yana sumbatar ta, (Harkar fa ta manya ce, nayi nan ni dai🏃‍♀️). Zeinabu na zuwa suka duba tukunya sai suka ga har dambun ya fara rusuna alamar zai d'auki dahuwa, ajiyar zuciya ta sauke tace "Ikon Allah, duk da ana cewa a daina yarda da canfi amma wani abun idan ka ganshi dole ka amince, to Allah ka gafarta mana." Lieutenant bai jima ba ya sake fita dan baya son Hajia ta saka masa na jiyamu, fitarshi kuma ta bawa Zeituna damar zuwa madafa aka k'arasa sauran aiki da ita, suna cikin jera kwanukan abincin Ummy ta dawo, wanka tayi ta fito lokacin har Hajia ta ci nata abincin ita kad'ai akan makeken teburin daya had'a kujera goma sha biyu, fitowar Ummy suma matan da su Hamna suka zauna suka ci na su abincin, a wurin ne Ummy ta dannawa Amar kira, bayan ya d'auka tace "Kana cikin gida ne?" Daga b'angarensu ya amsa da "Eh Ummy, kin dawo ne?" "Na dawo, ka jira yanzu za'a aiko miki da abinci." Amsawa yayi da "To Ummy." Tana aje wayar ta kalli Kamal dake kusa da ita tace "Ka shiga madafa abincinsu na nan a kula ka kai musu." Soueiba ce ta kalli Kamal tace "Daga nan ka duba ka gani ko Jibril yana nan sai su ci tare." Da kai kawai ya mata alamar to, Zeinabu ce ta kalleta tace "Yana ciki ai, na ga shigowar motarshi kuma har yanzu tana nan, tare da Junaid ma suka shiga." Soueiba ce tace "Ah to shikenan, ka kai musu kawai, kace idan ma bai ishesu ba sai su zo a k'ara musu, dan yau kowa ya wuni da yunwa saboda Amna yau ta hora mu." Dariya suka kwashe da ita banda Zeituna da tayi shiru tsananin mamaki ya k'ara rufeta, sai yanzu ne data shigo gidan ta fara fahimtar wata b'oyayyar rayuwa da suke, kowa d'an shi kawai ya sani bai damu dana d'an uwa ba, sannan ita kuma Ummy da take da yara biyu d'ayan kawai ta damu da shi, amma Ammar dake babban d'an ta bata nuna kulawa a kanshi ba, kuma ta tabbatar yana gidan dan ya riga sauran ma zuwa gidan, hakan yasa taji ba dad'i sosai ta mik'e daga kujerar ta nufi madafa, wani kwano ta samu madaidaici mai kyau ta zuba dambun ciki sannan ta samu k'aramin shi ta zuba had'in nik'akk'en naman da petit poit sannan ta fito, kai tsaye hanyar waje ta nufa ta kuma sa'ar had'uwa da Kamal ya dawo, kwanon ta bashi tace "Kamal, ka kaiwa yah Ammar kaji." Kallonta yayi yace "Aunty Zeituna, har yanzu yah Ammar zaki ci gaba da kiranshi?" Dariya tayi tace "To ya kake so na kirashi? Ai yayana ne a zahiri, ka je ka kai masa ka dawo." "To." Ya fad'a yana juyawa ya koma b'angarensu, yana zuwa wata sallamar ya sake yi ya shiga, kai tsaye d'akin Ammar ya nufa har Amar na fad'in "Autan Ummy ina zaka je?" "Wajen babban yaya." Ya fad'a ko juyowa baiyi ba, k'wank'wasa k'ofar d'akin yayi tare da turawa ya shiga, kwance yake yana kallon sama yayi nisa a tunani, har ya tsaya gabanshi ya aje kwanon k'asa bai kalleshi ba saida yace "Yah Ammar ga abincinka nan." A hankali ya kalleshi ya tashi zaune, kallon kwanon yayi ya sake kallon Kamal yace "Abinci na kuma?" "Eh." Kamal yace ya juya da niyyar fita, sake cewa yayi "Abinci fa? Wa yace ka kawo min?" Juyowa yayi yace "Aunty Zeituna ce, amaryar Abba." Bushewa yayi da dariya kamar mahaukaci sabon kamu, irin dariyar da yake yi ce yasa Kamal cewa "Yah Ammar lafiya?" Tsayawa yayi ta kalleshi yace "Ko da nace, ni nasan inba bak'o ba babu wanda zai aiko min da abinci, to naga dai ko uwar data haifeni bata damu da ci na ba bare kuma wanda suke kewaye da ita." Jinjina kai yayi yace "Amaryar Abba, amma me yasa zata aiko min da abinci?" Kamal ne yace "Ni ma ban sani ba." Da mamaki Kamal yace "Zaka ci kenan?" K'uri ya masa da ido yana kallo hakan yasa ya fita ya rufe mishi d'akin, yana ganin fitarshi ya shafa cikin da har kukan yunwa yake masa amma kasala ta hana shi fita ya je ya ci abinci, murmushi yayi yace "Zan ci mana Kamal, har na manta kalar d'and'anon abincin gidan mu, ina ma Ummy ce ta aikoka da abincin nan, da na ci da farin ciki da kuma karsashi ko da bana yanayin cin abincin, amma gashi matar data shigo gidan nan jiya wacce nayi mata kashedi akan uwata ita ce ta zubo abinci wai akawo min, duk da bansan manufarta na yin haka ba amma dai hakan yasa na ji kamar an kula dani ne." D'auko kwanon yayi ya bud'a, take yaji yawunshi sun tsinke, tashi yayi yaje ban d'aki ya wanko hanayyenshi ya fito, saida yayi bismillah tare da fad'in "A'u'zu bikalmatillahi tammat-min sharri ma kalaq." Duk yayi hakane dan aniyarta ta koma mata wai idan ma abinda ya mata jiya ne zaisa ta fara gaggawar d'aukar mataki akan shi. *A gurguje* Da magribar wannan ranar aka kawo kayan Amar ma, shi ma dai kamar yanda Ammar yayi haka ya kawo, sai dai ba shine ya kawo ba, wasu daga cikin yan uwa na dangin mahaifinsu da kuma abokan lieutenant ne suka kawo, anan kuma take kafin su tafi Hajia ta shaida musu nan da kwana goma sha hud'u sati biyu kenan za ayi bikin, dan haka a shirya da kyau kafin lokacin, da haka labari ya riski kowa inda aka shiga shirya ma wannan rana. Wani ikon Allah kuma tun daga wannan ranar kullum akayi abinci na rana da dare sai Zeituna ta fitarwa da Ammar, duk yaron daya tarbi gabanta shi take bawa yana kai mishi, lokacin da lieutenant ya fahimci haka kuma sai yace ta rabu dashi mana shi fa ba yaro bane, akan me ma zata damu da shi ne? Dariya kawai tayi tace tana yi ne saboda Allah, kuma taga shi bai damu da ya zo ya karb'a ba, Hajia ma baida habaici da cewa neman gurin zama ne babu abinda take fad'a mata, haka ma Ummy gani take wahala ce take ba kanta, indai Ammar ne wata rana ya gwasaleta, wannan shine abinda take fad'a, Ammar kuma kuma yanzu ya daina cin abincin waje inba na safe ba, ya sakankance yana cin wanda Zeituna ke aika musu, dan lokuta da dama tare da duka sauran yan uwan take aika musu musamman da dare lokacin duka sun dawo, Ummy da kanta ta shirya tare dasu Amna suka je madarunfa aka kaiwa Hadiza kayan Amna ta gani tasa albarka, data tambayi Ummy abinda za ayi ko ya rage sai tace babu komai da suke buk'ata daga wurinta, alfarma kawai ta nema na ta zo ran damu taga d'akin yarta hakan zaisa taji dad'i, a haka kuma ake ta shirye shiryen biki dan lokacin ya taho sosai. Wajen amare ma sun gama jarabawarsu sosai aka zage ana ta gyaransu kamar hauka, dan Hajia da kanta tasa ake musu gyaran, da farko suna zuwa ne a musu, amma daya rage sati d'aya sai mai musu gyaran take zuwa gida tana musu, kuma a haka yaran zamanin suma amaren suke k'arawa kansu wani had'in wanda suka koya, Ummy ma haka ta zage tana dafa musu kaji tunda ta ga sauran sati d'aya, da haka har aka riski daren da za'a saka amare lalle. Duk iyayen na zaune akan teburin cin abinci suna ci suna hira, kuma hakan ya faru ne saboda Alhaji na wurin, ba dan haka ba babu wanda ya isa ya cika Hajia da surutu alhalin tana cin abinci, Amar ne ya shigo tare da Ammar kamar wasu zakuna, Amar ne yayi sallama suka nufi kan teburin yana gaishe da mutanen wurin, Ammar na zuwa hannu ya zura gaban Hajia ya d'auki robar ruwan da take sha ya kifa bakinshi yasha sosai, kowa kallonshi yake har da ita kanta Hajiar, saida ya sauke robar ya kalli kowa dake wurin shima yana murmushi, lokacin da kallonshi ya sauka kan Zeituna wacce kanta ke k'asa ne ya fad'ad'a murmushin shi yace "Ina wuni." Da sauri ta d'ago kanta lokaci d'aya kuma ta mayar dashi k'asa dan bata zaton da ita yake, duk wanda ke gurin kallonshi sukayi da matuk'ar mamaki, *yau Ammar ne ke gaishe da wani?* gaisuwar ma ga wacce ba'a tsammanin zai iya gaisheta, ganin irin kallon da suke mishi yasa ya sake kallon Zeituna yace " Dake fa nake, *uwa*." Sake d'agowa tayi cike da tsoron abinda zai iya fad'a mata, suna had'a ido bata san lokacinda tace "Yah Ammar ina wuni." Murmushi ya mata yace "A'a uwa, ki kira ni Ammar kawai, ko kuma ki kirani da *d'an ki*, tunda ke ma uwata ce." Wata irin dariyar rainin hankali Hajia ta bushe da ita har da gaggab'awa take, wani kallo Ammar ya mata kafin ya kalli Ummy yace "Ummy ina amaryata take? Ina so zamuyi magana ne." Hararan sama da k'asa ta masa taja dogon tsaki, mayar da kallonshi yayi kan Zeituna yace "uwa dan Allah zaki iya fad'a min inda take?" Zeituna da ita dai al'amarin d'an mijin nata ke tsorata ta da sauri tace "Tana d'akin..." Da sauri Ummy ta katseta da cewa "A'a Zeituna, rabu dashi kawai, uwar me zai bata yanzun?" Tab'e baki yayi ya kalli Zeituna yace "Uwa zan iya baki sak'o wurinta?" Kamar sakarai haka take kallonshi baki bud'e ta jinjina masa kai alamar eh, da hannu ya mata alama yace " Zo to, sirri zamuyi." Mik'ewa tayi tsaye zata tafi lieutenant ya daka mata wata harara yace "Wai ke me yake damunki ne? Kanki d'aya kuwa ko kuma ke ma irinshi ce?" Alhaji ne yace "Babba, ka barta dan Allah." Murmushi Ammar yayi yace "Abba kwantar da hankalinka mana, babu inda zan tafi maka da matarka, nima fa uwata ce." Wata harara lieutenant ya wurga masa wanda tasa Ammar kwaso shoki, har zai sauketa akan idon lieutenant sai kuma ya juya ya kalli Amar dake gefenshi ya watsa mishi ita a fuska, Zeituna na zuwa kusa dashi saida ya k'ara matsawa kusa da ita ya juya baya suka bawa mutanen baya kafin ya sassauta murya yace "Uwa ki samu Amna a d'aki ki fad'a mata ta baki kayanta ki kawo min za'a d'auki awonta ne (mesure)." Jin abinda ya fad'a yasa Zeituna sauke ajiyar zuciya ta kalleshi tace "Toh." Da sauri ta juya ta nufi d'akin Ummy inda amaren suke, tana shiga ta same su tare da wasu daga cikin k'awayensu, gabanta ta tsaya tace "Amna, sak'o daga angonki wai ki bado kayanki za'a d'auki awonki ne." Kallonta tayi tace "Yah Ammar? D'inkin zai min?" Da murmushi ta amsa mata da "Ni ma ban sani ba, tashi ki d'auko kawai." Mik'ewa Amna tayi ta fito Zeituna na biye da ita a baya, d'auko mata kayan tayi ta bata ita ma ta juyo dan kawo masa, tana zuwa ta same shi tsaye kusan Hajia sai kallonta yake, ita kuma ta had'e fuska sai hararenshi take, Amar dai dariya yake musu har yace "Dan Allah Hajia ki ci abincinki kar ki biye masa, so fa kawai yake ki biye masa kuyi fad'a." Tab'e baki tayi tace "To ai yanzu ni ya daina bani wahala shalele, ka rabu dashi zaiyi ya bari ne inya gaji." Da wani murmushi a fuskarshi yace "Da gaske Hajia? To zan gani." Zeituna na bashi kayan a leda ya karb'a ya matse ledar a hammata, ba zato ba tsammani ya daddage ya samu hak'ark'arin Hajia ya danna mata cakulkuli, ( Hajia mutan makka😂), ai wata zabura Hajia tayi daga kan kujerar tare da sakin ihu har cokalin hannunta ya fad'i abincin cikin cokalin ya zube, haba wa ai sai Amar ya fashe da dariya tare da taimakon Alhaji da Husseina, Ummy kam da Zeinabu da Soueiba duk rufe bakinsu sukayi suna toshe dariyarsu, Ammar da tuni ya zura a guje shima dariyar yake, yana kaiwa bakin k'ofar fita daga gidan ya had'e da Hamna ta shigo tare da k'awar ta wacce ya amshi lambarta, tsayawa yayi suna kallon juna da ita b'angare d'aya kuma yana kallon Hamna da wutsiyar ido, washe baki tayi tace "Lah mai kyau, sai ganshi dai yau mun had'u, dama kuma ina son ganinka dan naji dalili da yasa baka kirani ba." Yanda ta kafeshi da ido alamar tana jiran amsa yasa yayi murmushi ya kalli Hamna yace " Hum! Kinga ranar da kika bani lambar nan, saboda ina tuk'i daga na bawa k'awarki ta saka min sunanki akai, sai kawai tace min wai ta goge, to har yanzu ina so na sani ne gogewa lambar tayi ko kuma gogeta akayi, shine abinda na kasa fahimta." Wani marairaicewa yayi yace "Dan Allah budurwata ki tayani tambayarta ta fad'a min, na shiga damuwa sosai saboda rashin kiranki da banyi ba, da zaran na kwanta bacci ke nake gani a idona, idan ina wanka ma ke nake ji kamar kina goga min bay..." Hamna ce ta fizgi hannunta tana fad'in "Dallah *Ami* wuce mu tafi, k'arshen marar kunya ne wannan yanzu saiya fad'a mana abinda kanmu ba zai iya d'auka ba." Juyowa yayi ya bita da kallo yace "Kunya? Ai laifinku ne inma bana da kunyar, tunda sanda ake rabonta ina bacci kuma babu wanda ya tasheni." Tsaki Hamna tayi wanda yasa ya juya da hanzari ya kamo k'aramin kallinta, duk da ta tsorata da yanda ya fizgota ya kuma kalleta da jajayen idonshi hakan bai hanata cewa ba "Dallah malam sake ni, ni yanzu sam bana son had'a hanya..." Bai bata damar k'arasawa ba ya kama dogon hancinta yaja sosai, siririyar k'ara ta saki take idonta suka kawo ruwa saboda zafin da taji, k'ank'ance idonshi yayi yace "Na sake jin tsaki ya fito daga bakinki zuwa kaina wallahi zaki rasa hak'oranki." Sakinta yayi ya juya zai fita Ami tace "Mai kyau." Tsayawa yayi ya juyo a hankali ya kalleta, matsowa tayi tace "Nace ka kawo wayar taka saina saka maka lambar ko?" Saida ya kalli Hamna yace "Ki barshi kawai, wacce ta goge lambar uta zata sake bani ita da kanta." Yana fad'a ya juya ya fita ita kuma ta kalli Hamna tace "Dan Allah besty ki bashi lambar, wai ko dai ba kya so na auri yayanki ne?" Dafe goshi Hamna tayi ta mata kallon sakarai tace "Ki farka idan ma bacci kike, nan da kwana uku za'a d'aura aurenshi da Amna." "Me?" Ta fad'a da d'an k'arfi, kallon k'ofar daya fita tayi tace "Amma kuma alamunsa bai nuna haka ba." "Shi wani irin mutum ne da ba'a gane gabanshi da bayanshi, k'ok'arin sanin asalin Ammar zai iya tarwatsa miki k'wak'walwa, dan haka ki fita a harkarshi kafin ya fad'a miki abinda zaisa kiyi nadamar sani na a rayuwa, dan ko kad'an bashi da tabbas." Jinjina kai kawai tayi suka shiga ciki. *Da asuba*... *Alhamdulillah* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _31_ *Kubra* wacce take kamar 'ya ga Alhaji ce ta zo gidan dan shafe amare da angaye da lalle, d'aya bayan d'aya ta shafawa amaren kafin ta nufi b'angaren samari, d'akin Ammar ta fara turawa a hankali, cikin sa'a k'ofar ta bud'e ta shiga cikin sand'a, amma saita samu Ammar zaune akan sallaya ya tank'washe k'afafunshi, d'agowa yayi yana kallonta da mamakin shigo mishi d'aki a wannan lokaci, ita ma kallonshi take ganin bacci pal a idonshi alamar bai samu baccin ba, murmushi ta sakar mishi tare da matsawa kusanshi rik'e da robar lallanta tana fad'in "Ammar idonka biyu? Ai na d'auka zan samu kana bacci ne ta yanda zan wankeka da lalle." Saida ya kashe mata kyawawan idanunshi kafin yace "Wanda bai ga annabi ba kuma ina shi ina bacci?" Wani murmushin ta sake yi tace "Hakane, to naga hannunka." Kallonta kawai yayi bai bata hannu ba hakan yasa ta d'ebo lallen ta nufeshi da nufin shafa mishi a kai, da sauri ya mik'e tsaye yana rik'e farar jallabiyarsa ya dakatar da ita yace "Tsaya aunty Kubra, kar muyi haka dake fa, me zaki min da wannan sai kace wani mata-maza?" Gumtse bakinta tayi tace "Lalle zan shafa maka, kuma dai kasan sai an shafa maka ne kad'ai zai baka damar angwancewa da yarinyata ko?" "A al'adarku ba." Ya fad'a cike da gatsali kafin ya d'ora da "Nuna min ina ne za'a shafa sai ki ban na shafa da kaina, gaskiya bana so jikina ya b'ace da wannan abun." Tab'e baki tayi tace "Naga yanda za kayi wanka da ruwan lalle kam." Lallen ta d'ebo a hannu ta mik'o mishi, yamutsa fuska yayi kamar yaga kashi tare da saka yatsarsa manuniya ya lak'ato lallen ya kalleta yace "Ina zan shafa to?" "A kai." Ta bashi amsa, a hankali ya d'an shafa shi a saman gashi tare da kallonta alamar tambayar sai ina, saida taja tsakin jin haushi kafin tace "Sa a tafukan hannayenka." Shima juya idonshi yayi suka kalli sama cike da birgewa tare da cewa "Kamata yayi ace mata kawai ke wannan abun, amma maza abun ba tsari." Wanda ya d'an rage a yatsarshi ya murje a tafukan hannayen yace "To aunty Kubra ni ma dai na shiga lalle, shikenan?" Juyawa tayi ta fita tana fad'in "Amaryarka dai ta shiga, amma kai kam har yanzu da saura, in baka sake shafa lalle ba ko na wanke 'yar sai dai na kaita d'akin wani amma ba kai ba." Murmushin gefen labb'a ya mata ya bita da cewa "Aunty Kubra kenan, idan ma kinyi haka da kanki ne zaki dawo da ita ai, dan sai nayi abinda da kanku zaku je ku d'auko ta ku dawo da ita hannu na." Tana fita ya fad'a ban d'aki ya wanke kanshi da hannayenshi ya fito ya rufe d'akin shi ya tafi masallaci. Kasancewar yau ba zai fita da wuri ba yasa bai dawo daga masallaci da wuri ba, inda amare su kuma safiya na wayewa kowace ta shirya dreba ya kaisu gidan da zasuyi wunin k'umshi, da k'yar Ummy ta had'a kan Amna da Hamna suka tafi tare dan har yanzu ba wani shiri suke ba, kusan k'arfe *08:24* ya shigo gidan, kai tsaye falon Hajia ya nufi, Hajia na zaune Husseina gefenta sai Ummy dake rubuta duk abinda Hajia tace mata wanda zasu buk'ata saboda hidimar, shigowarshi tayi daidai da fitowar Zeituna daga madafa rik'e da robar yaghurt d'in da yasan Hajia kad'ai ke shan ta a gidan saboda rashin zak'inta, abun mamaki yau ma dai kai tsaye madafa ya nufa amma kuma yana fad'in "Uwa kin tashi lafiya?" Cike da nutsuwa da kuma girmamashi ta amsa da "Ina kwana, antashi lafiya?" "Lafiya lau." Ya fad'a yana shigewa madafar, Zeituna na zuwa ta sunkuya ta bawa Hajia madarar, tana karb'a ta juya ta nufi madafar ita ma, a cikin ma'ajiyar (store, mangaza) kayan abinci ta ji motsinshi dan haka saita shiga sarrafa indomie da k'wai, yana fitowa da carton d'in lemu a hannunshi dan ya saka a fridge ya ganta, kusanta ya matsa yace "Uwa girki ake yi?" Ba tare data kalli k'wayar idonshi ba tace "Eh, na ga baka fita bane, shine zan d'ora maka indomie." K'ura mata ido yayi yana kallo kamar mai tunani kafin yace "Uwa, meyasa kika damu da bani abinda zan ci ne? Alhalin ni ban buk'aci haka ba, kuma ina da wayon da zan iya nemawa kaina idan ina buk'ata? Meyasa?" Har yanzu ma ba tare data had'a ido dashi ba saboda kwarjinin da yake mata tace "Yah Ammar ba saida wani dalili sannan zan kyautata maka ba, kawai naga kai baka neman abincin ne alhalin akwaishi, sannan kuma babu mai tambayarka ka ci ko baka ci ba, sannan ko da anbayar a kaiwa 'yan uwanka babu mai cewa ku ci tare, shiyasa nake tunanin ko kai d'in irin mutanen nan ne da basu damu da cikinsu ba." Take Ammar yaji hawaye na neman taho mishi saboda abinda ta fad'a, matar uba na! Matar dana rainawa k'ura wai ita ce ta damu da cikinshi har haka! Shi kam wai me yayi wa iyayenshi ne har haka da zafi? A k'alla ba'a k'asara ba yafi shekara d'aya da rabi rabon daya ci abincin gidan nan idan ka cire ruwa lemu, amma sau d'aya Ummy bata tab'a tambayarshi ya ci ko bai ci ba bare tace ya ci, sake kallonta yayi yana murmushi yace "Nagode Uwa." Ita ma murmushin tayi duk da kanta na kallon k'asa tace "Ba komai." Juyawa yayi zai fita har ya kai k'ofa ya dawo tare da cewa "Uwa zaki min wani taimako?" Kallonshi kawai tayi alamar tana saurare kafin yace "Dama su Amar sun shirya zama ne a k'ofar gidan nan ranar biki, kuma sunce dole zamu gayyaci duka abokanan mu, har ma mun riga da mun had'a kud'in da zamu bayar a mana girki, shine nake so na ware nawa daban dan ni ba anan zan zauna ba, ko zaki iya mana girkin da zamu ci?" Juyowa tayi sosai tana kallonshi da mamaki tace "Amma yah Ammar me yasa kai ma ba zaka zauna tare da 'yan uwanka ba? Ina ganin kamar hakan zaifi armashi tunda kai ma ka bayar da kud'in ka." Murmushi yayi cike da nutsuwa yace "A'a, ina so na ware kaina ne." Jinjina kai tayi tace "Shikenan, za ayi insha Allah." Da farin ciki yace "Yawwa uwa, amma fa bana so kowa ya sani." Jinjina kai kawai tayi ta ci gaba da girkinta shi kuma ya fita. Tunda Zeituna ta shiga madafa Hajia tayi tsaki tace "Aikin banza, ni bansan meye manufar yarinyar nan akan waccen yaron ba, Allah yasa dai ba jan hankalinshi take son yi ba suja min abun kunya." Da sauri Husseina tace "A'u'zu billahi, haba Zeeya'atu, me yasa zaki fad'i haka kema kamar wata k'aramar yarinya? Dan Allah ki dinga kyautatawa mutane zato, kuma idan ita kince baki san halinta ba duk da shekarun data kwashe tana miki bauta, ai shi Ammar kinsan me zai iya yi da wanda ba zai iya yi ba." Wani d'an iskan kallo ta mata tace "Ina ce dai bansa dake a maganata ba, to akan me zaki tsoma mi bakinki? Kuma da kike fad'in haka ke kinsan halin Ammar d'in ne? Yaron da rashin kunyarshi ta bunk'asa ta yanda har gaban iyayenshi zai iya fad'in abinda yake so, shine kike so na kyautatawa zaton? Ke zaki iya rantsewa cewa Ammar baisan 'ya mace ba?" Girgiza kai tayi tace "Allah ya shiryaki, amma ni dai har zuciya ta na yarda da Ammar, shi kawai yaro ne mai k'iriniya mai kuma fad'in gaskiya duk a yanda ta zo, sai dai kar kowa yaji dad'i amma hakan bai dame shi ba." Hararanta Hajia tayi ta mik'e ta nufi k'ofar fita tana fad'in "Shiyasa na tsani ina zaune a zo duk a cika min falo, inba sa ido ba ga d'akinki ki zauna mana." Dreba ta samu ta bashi takardar da aka rubuta mata abun buk'atarsu tace "Ka samu Hassan zai baka kud'i ka siyo mana duk abinda ka gani rubuce anan." Da ladabi ya amsa da "To Hajia, insha Allahu." Juyowa tayi shima ya juya ya fita dan isar da sak'onta. *Zuwa yamma* gida ya fara nuna alamun ana hidima kuma babba, domin kuwa kujeru ne aka cika gidan dasu aka jerasu gwanin sha'awa, sannu sannu mutane suka fara hallara har gida ya fara batsewa, b'angare d'aya babbar redio ne aka kunna yana tashin kid'a, ana cikin haka amare suka dawo daga wurin wunin k'umshi, tubarkallah yanda gidan ya cika kai kace yau ne bikin, a haka kuma wankan amare ne kawai za ayi, kuma yawan mutanen ya samo asali ne saboda kowane b'angare da na shi dangi, dan haka gida ya cika mak'il har aka shirya amare aka tafi wurin wanka a gidaje daban daban, sai bayan magriba aka dawo da amare gida. Shiri na musamman aka musu kowace a cikin tsadadden leshe na gani na fad'a, Amna dake cikin leshenta kalar pink tayi masifar kyau, a haka aka fito dasu wajen bidirin bayan an turaresu da turaren jiki, duk da rincab'ewar da wurin yayi ana fitowa dasu kowa ya mayar da kallonshi kansu, Umaimah ce a gaba sai Jamila tsakiya, Amna na baya tare da Hamna wacce ita ma ke cikin leshe kalar na Amna sai dai d'inkin ya banbanta da kuma shirin, amma daga d'aurin kallabi da jaka da takalama sark'a da yan kunnai duk iri d'aya ne, amma kwalliyar fuskar Amna da kuma ashaokin dake kafad'ar ta ya banbantasu, Hamna kuma yanda d'inkin ya fito da ita da manyan d'uwawunta ga uwar atach d'in data gabza akai kamar tayi magana tasha kitso, d'aurin d'an kwalin kusan saman rabin kanta ne kawai yake, hakan yasa zaka iya gane kitson dake kanta da kuma kitso k'waya d'aya da alayi da kalar bleue d'in atach. Akan kujeru aka zaunar dasu inda Hajia ke tsaye gabansu ta kalli su Zeinabu tace "Ku fito da yayanku." Wani kallo Zeinabu ta mata a ranta tace "Kaji wai mu fito da yayanmu , mazan fa take nufi." A zahiri kuma jinjina kai tayi tace "To Hajia." B'angaren samarin ta nufa ita kad'ai, tana zuwa ta shiga da sallama saboda k'ofar bud'e take da abokanansu ciki, tana shiga suka gaisheta kafin tace su fito, nan suka fito suna ta ihuce ihuce da tsokanar angayen irin dai rahar nan ta samari, suna zuwa Junaid ya tsaya ya turo Amar gaba yana fad'in "Ku wuce ku, ni ina nan tunda babu sarauniyar sai sarki kawai." Gwalo Amar ya mishi yace "Gwauro kenan, mu dai munji dad'in mu." Ammar dake bayansu ya k'urawa Hamna ido haushi na kashe shi a wurin, tambaya ya ma kanshi "Akan me Hamna zata fito haka babu mayafi? Me yasa za tayi shiri kamar amarya ita ma?" Hajia ce ta juyo garesu tana musu kallon ku taho mana, dukansu k'arasawa sukayi suka zauna har da Junaid d'in dan har da kujerarshi a ciki, haka suka jera su bakwai a wurin masha Allah, kamar yanda Hamna ke bayan yar uwarta tsaye kamar wata mai tsaronta, hakanne yasa Ammar d'ago kanshi ya kalleta yace "Ke dan ubanki fita daga kaina, kin min wani k'arere dake a baya." Amna da kanta ke k'asa a hankali ta saci kallonshi, masha Allah ta fad'a a ranta ganin wani kyau da yayi cikin chadda kalar ruwan k'asa, karin hular shi da yanda ta zauna mishi a kai sun masifar dacewa da fuskarshi, ga uwar k'asumbarshi dake ta k'yalli alamar tasha gyara, mayar da kanta k'asa tayi yayin da taji Hamna na fad'in "Malam babu ruwanka da tsayuwata anan, dan kai na tsaya ba dan yer uwata ne, idan zan tsaya anan dan kai ne wallahi sai dai dan na zama ajalinka ne." Lumshe ido Amna tayi jin har yar tsamarsu ta kai haka, inda Ammar ya gumtse baki yana mata murmushin iya shege ya sake kallonta yace "Idan naje lahira zan siyo miki kankana, nasan ta can tafi tanan komai, asha a k'ara zak'i." Kashe mata ido d'aya yayi tare da yi mata gwalo, haushi ne yasa Hamna tunzura ta zura hannu ta ture hular dake kanshi ta fad'i, da fari a hassale ya kalleta da niyyar aikomata ashar, amma ganin fuskarta a had'e sai kawai yayi niyyar yin maganinta cikin ruwan sanyi, Husseina ce tace "Ke Hamna lafiyarki kuwa, ya zaki ture hular ango?" Hassana yar uwar Husseina ce ta d'auko hular zata saka mishi tana fad'in "Ai kinsan halinsu, in suka had'u kamar b'era da mage suke." Da sauri ya janye kanshi yana wani shak'iyin murmushi yace "A'a Hajia bana so, tunda dai k'anwar matata tace hular nan bata min kyau ba to na hak'ura da ita." Hassana ce ta kalli Hamna data saki baki tana kallonshi tace "Ke kuma ina ruwanki da shirinshi to? Kika sani ko ya ma amaryar ita?" Ammar ne yace "To ai Hajia nasan ita ma bata mata ba, ko kin manta yan biyu ne? Zuciyarsu ma d'aya ce." Tsaki Hajia tayi ta matso kusansu ta dungurar mishi kai tace "Shege uban surutu, a wajen hidimarku ma ba zaka rufewa mutane baki ba, idan ka b'ata min rai sai dai ka bar wurin nan ba tare da an maka wankan turaren ba." Murmushi ya mata yana dafe da inda ta rank'washeshi yace " Babu fargaba a tare dani, a cikin dangina nake wanda nasan zasu iya yi min." Wani tsakin ta kuma yi ya bi bakinta da kallo yace "Hajia, Allah ja-leb'en nan da kika shafa ya miki kyau, ki daure dan Allah ki sumbace ni ko sau d'aya ne, kar ya fita a banza baki sumbaci baki na ba." Husseina da Hassana dariya suka saka hakan yasa ran Hajia b'acewa dan har yanzu ba k'aunarsu take ba, kwalaben turarukan dake hannunta masu matuk'ar tsada da k'amshi ta jefa mishi a k'irji ta juya da sauri ta bar wurin rai a b'ace, ganin haka da Ummy tayi ta tabbatar Ammar yayi halin, duk da bata ji me ya faru ba amma tasan aikinshi ne, girgiza kai tayi ta wurgo mishi da harara daga inda take, Hamna da har yanzu ke bayansu ce tace "Kaga bak'in halinka ya fara shafar yer uwata tun yanzu, gashi kasa Hajia ta tafiyarta bata fesa muku turarukan ba, anji sanyi dai wallahi." Ba tare daya kalleta ba tace "To ai bana da bargon rufa ne, kuma kinga kune da jin takaici bani na ba, tunda babban abun kunya ne ace babban jikan Alhaji Suley baya da bargon rufa idan yana jin sanyi." Hannun Amna ya kamo ya matse sosai yana murzawa ya kafeta da ido yace " Amna, nasan kinsan wanene ni, kuma a haka kika amince da zaki aure ni, hakan na nufin kenan zaki iya zama dani a duk yanda nake?" Kallonshi Amna tayi yayin da take lumshe idonta a hankali wanda suka sha dogon gashin daya dace da idonta ganin sha'awa, wani sauk'akk'en murmushi tayi ta d'an gyad'a mishi kai alamar eh, murmushi ya mata wanda ya k'ara bayyanar da kyawunshi yace "Karki damu to, *insha Allahu da sannu zamu samu masu son mu a duk yanda muke*." Yana fad'a ya juya kanshi a hankali ya kalli inda Ummy ke tsaye, suna had'a ido ta kawar da kanta tana jan tsaki, murmushi yayi ya d'auke kanshi, duk abinda ya faru a idon Zeituna, da sauri ta matso ta d'auki turarukan da suka fad'i k'asa ta mik'awa Husseina tace "Hajia ke ki fesa musu mana tunda Hajia ta tafi." Girgiza kai tayi tace "Aa 'yar nan rufa min asiri, a gaskiya ina so ayi bikin nan lafiya a gama lafiya, bana son abun magana." Hassana ce tace "Kira Sa'ada mana saita fesa musu, ita ya dace ai dama." Husseina ce tace "Ko kuma Zeinabu ba ko Soueiba." Kallon inda su Zeinabu suke tayi ta taka da niyyar zuwa ta kai musu turarukan amma abun mamaki sai Zeinabu ta dakar da ita tace "A'a gaskiya, su Hajia ma sun saka bare kuma mu, auren 'ya'yanmu ne za ayi, gaskiya karki ja mana jarfa." Tsayawa tayi da mamaki tana kallonsu, ya zatayi kenan? Muryar Ammar taji yace "Karki damu amaryata, ni wannan ba sabon abu bane a wurina, ke kawai nake so kema ki samu k'arfin gwiwar daurewa da shanye komai." Tana jin haka ta juyo cike da jin haushin halayen yan gidan nan ta zo kusansu, tana zuwa ta fara bud'e kwalaben, fesa musun data fara yi yasa kowa kallonta da mamakin katsalandan irin nata, sai dai babu mai magana domin kuwa matar lieutenant ce, kallonta Amna tayi tana murmushi shima kuma Ammar haka, cikin taushin murya yace " *Uwa ita kad'ai ce mai tarar aradu da kai ko da me zai faru in dai akan 'ya'yanta ne, a ido na girmeki a shekaru, amma halayyarki da d'ab'iarki sun gama d'ad'ani a k'asa ta yanda dolena na d'auke ki a matsayin uwata*, mun gode da kulawa." Hannu yasa ya karb'i turaren ya karb'a yace "Duk d'a na gari ba zai so ganin ana cin zarafin mahaifiyarshi ba, dan haka nima ba zan juri ganin waccen masassar cizon sauron tana miki ihu ba, ki barshi kawai mun gode." Baki sake kowa ke kallonshi da mamakin sunan daya kira Hajia da ita, Jibrl wanda Jamila ta shiga tsakiyarsu ne ya zuro kai yace " Kai Ammar kaji tsoron Allah, yanzu Hajiar ce haka?" Hassana ce tace "Wai dama Hajia yake nufi? Yanzu Ammar kakar taka ce kake kira da wannan sunan?" Had'e fuska yayi yace "Hajia muna irin haka dake ne?" Girgiza kai tayi tace "A'a." Sake cewa yayi "To kina so mu fara irin haka dake?" Nan ma kai ta girgiza tace "A'a, Allah huci zuciyarka." Mik'ewa yayi tsaye ya saita kwalbar turaren jikin Amna ya fara mata wanka dasu, Husseina dake rik'e da wani kaskon wuta mai kyau tana turaren wuta bata san sanda ta kai hannunta kan wutar ba saboda kallonshi da take, da sauri ta janye hannunta ba tare data daina kallonshi ba, saida ya mata sharkaf da turare kafin ya mik'awa Zeituna kwalaben ya juya ya bar wurin ko a jikinshi, Hamna ma dake tsaye har yanzu ce tana yamutsar fuska saboda a cikin turarukan daya fesa akwai wanda ya tayar mata da zuciya, juyawa tayi ita ma ta bar wurin, Ummy da duk wani motsin Hamna ke kanta tana ganin haka ta bi bayanta, a falo ta sameta ta zauna tana shan ruwa, zaune tayi ita ma tana kallon mutanen dake kai kawo a falon har zuwa farfajiyar gidan tace "Ya naga kin zo nan kin zauna kuma? Da wata matsala ne?" Cikin yamutsa fuska tace "Ummy bana jin dad'i ne, gaba d'aya turaren da yah Ammar ya fesa ne ya tayar min da zuciya." Take gaban Ummy ya fara fad'uwa taji zufa na neman karyo mata, haka ma fitsari ne taji kamar zai taho mata a guje, kallonta tayi yace "Baki da lafiya ne?" "Lafiyata lau Ummy, amma d'azu muna wurin wankan nan jiri ne ya dinga kwasata wallahi, shiyasa ma na koma mota na zauna." A firgice Ummy ta kalleta tace "Hamna! Yaushe rabon da kiga hannunki?" Kallon Ummy tayi ba alamar damuwa tace "Watan daya wuce." Cikin d'aga murya tace "To wannan fa?" Da wani murmushi a fuskarta tace "Ban gani ba, amma dai..." Tsawar da Ummy ta mata tana fad'in "Hamna shashashar ina ce ke?" Hannunta ta kama da k'arfi suka nufi d'akin ta, suna shiga ta wurgata kan gado ta bud'a wata ma'ajiya ta d'auko wata k'aramar roba mai kyau fara mai murfi ta bata tace "Maza shiga ban d'aki ki bani fitsarinki." Tsaye ta mik'e tana kallonta da alamar tambaya, da yatsa ta sake nuna mata k'ofar ban d'aki tace "Jiranki nake." Wucewa tayi inda Ummy ta fara safa da marwa a falon tana sharar zufa, cikin sanyin jiki Hamna ta fito ta mik'awa Ummy robar, hannu tasa ta karb'a ta bud'e magwajin (Gtest) ta saka, mik'a mata robar tayi ta koma ban d'aki ta zubar, Ummy kam idonta na kan wannan abun gwaji addua'r ta d'aya shine kar ya nuna abunda take tunani, inhar ya nuna kam ta shiga uku ta lalace. _Idan har kukayi comment sosai zaku sake ganin sabo zuwa gobe da yardar ubangiji._ *Alhamdulillah* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _32_ *Jan layi biyu* shine abinda ya nuna, tana rintse ido taji hawaye sun kwaranyo mata, bud'e baki tayi tana so tayi salati kuma ta kasa, shiru d'akin ya d'auka inda Hamna ta k'ura mata ido tana karantar yanayinta, ganin sai zufa take yasa ta taka kusa da k'ofa ta kunna mata ac ta juyo ta dawo tace "Ummy lafiya? Me yake faruwa?" Girgiza kai Ummy tayi ta bud'e idonta da k'yar wanda suka mata nauyi, gaba d'aya d'akin ne taga yana juya mata kamar zai kifata k'asa, hakan yasa tayi saurin matsawa jikin gado ta zauna tana dafe kai, ita ma zaunawa tayi ta dafata murya a raunane tace "Ummy dan Allah ki fad'a min meke faruwa?" Saida ta sake lumshe ido tace "Hamna, ciki ne dake, ciki Hamna, cikin Ammar jikinki, Hamna na shiga uku na lalace, ban san ina zansa kaina ba, Hamna ki tayani rok'on mutuwa kafin lokacin da kowa zai san abinda ke faruwa..." Kukan daya ci k'arfin ta yasa dole tayi shiru ta fara rizgar kuka, Hamna data daskare a wurin kamar an zuba mata ruwan sanyi, ta nema hawaye a idonta ta rasa, zuciyarta ta cunkushe ta yanda taji ta kasa maganar zuci ko tunanin abunyi, ta rasa fahimtar yanayin da take ciki, farin ciki? Ko bak'in ciki? a lokacin sai taji tafi tausayin Ummy ma fiye da ita kanta, dawowa tayi hayyacinta ta fara rarrashin Ummy tana fad'in "Ummy ki daina kuka, wannan *ita ce k'addarar mu*, mu rumgumeta hannu bibbiyu Ummy, mu mayar da al'amarin mu ga Allah shi zai mana mafita." Kallonta Ummy tayi tace "Hamna na daina kuka fa kike cewa? To me zanyi inba kuka ba? Ciki fa nake fad'a miki kina da, ko dai ba kya fahimta ne? Cikin d'an mutum ne jikinki cikin haihuwa, wanda kika samu sanadiyar kwanciyar da Ammar yayi da ke, ki fahimci tashin hankalin da muke ciki mana." Kawar da kai tayi tace "Tashin hankalinmu na yanzu ba shi zai hana mu shiga na gaba ba, zaifi kawai mu tanada kukanmu a tashin hankali na gaba." Tsayawa tayi da kukanta ta kalleta, tabbas abinda ta fad'a hakane, to kenan ya zasuyi? Hajia kullum son ganin laifinta take ta yanda zata tozarta ta, a girman laifin data aikata ma a yanzun zata iya sakawa lieutenant ya saketa, dan haka ta mik'e tsaye tace "Zan samo mana mafita Hamna, wannan abun ba zamu bari ya fito ba, ke dai ki ci gaba da b'oyewa kar kowa ya sani, zuwa gobe zamu san abunyi, yanzu mu fita kar a d'auka wani abun muke." Mik'ewa tayi tana kallonta tace "Ummy me zakiyi? Dan Allah ka da ki saka kanki a had'ari saboda ni, kawai ki bari kowa ma yaji, k'addara ce wacce babu wanda ya isa ya kauce mata." Hannunta ta kama tace "Ke dai mu tafi, ai ba kowa zai fahimci haka ba, hakk'i na ne Hamna na kula da ku, amanarku aka bani." Fita sukayi aka ci gaba da hidimar dasu, sai dai ko kad'an babu walwala a tare dasu, Hamna kuma dake tare da k'awayen ta wanda ta gayyata lokaci bayan lokaci saita shafa cikinta, a hankali take furta kalmar "Ciki." Da haka aka gama shagalin yau sai kuma na gobe idan da rai. *Washe gari* Tunda asuba Ummy ta samu Hamna suka keb'ea farfajiyar gidan, saida ta gyara hijabinta da tayi sallah dashi tace "Ummy lafiya kika kirani yanzu?" Kallonta tayi sosai tace "Hamna bacci kikayi wai?" D'an turo baki tayi gaba ba tace komai ba, murya k'asa k'asa tace "Hamna, na samo mana mafita, amma kiyi alk'awari zakiyi duk yanda na ce?" Cike da sangarta tace "Ummy ina ji, bacci fa nake ji har yanzu." Da tsantsar mamaki Ummy ta kalleta tace "Hamna anya kuwa kinsan abinda kike yi, gaba d'aya fa kina nuna kamar abun bai dameki ba." Take fara'arta ta d'auke ta kalli Ummy tace "Ummy raba dare nayi ban iya rintsa ido na ba, tunani na yafi karkata kan yanda yer uwata zata d'auki al'amarin idan taji." Cike da damuwa Ummy tace "Hamna dole ne ki tuna yer uwarki a wannan halin, amma ni nafi tunanin wani abun daban, kinsan me nafi tunani?" Girgiza kai tayi alamar a'a, ci gaba tayi da cewa "Hamna Hajia, kinfi kowa sanin yanda ta tsani d'an da bai fito ta hanyar aure ba, domin kuwa saboda hakane ma kika ga tana nunawa kawunku Labaran k'iyayya har da ma yayanshi, kiyi tunanin hukunci ko matakin da zata d'auka, ga kuma kawunku wanda jin hakan ba zai masa dad'i ba, sannan Ammar, Hamna a tak'aice bansan wane kallo zai yiwa al'amarin ba, ina tsoron abinda zai iya faruwa." "To Ummy yanzu meye abunyi?" Saida ta kalli k'wayar idonta sannan tace "Hamna zan karb'i cikin nan naki, ma'ana ni ya kamata kowa yasan inada ciki, bayan kin haihu saina karb'i abinda kika haifa kamar ni na haifeshi, in kuma ba haka ba Hamna sai dai a zubar da cikin nan tun kowa baisan da maganarshi ba." Wani irin tsamm taji jikinta yayi, sai yanzu ne ta gane girman al'amarin daya tunkarota, maimakon tace wani abu saita fashe da kuka ta rumgume Ummy, ita kanta Ummy kuka ta sanya, sun fara rera kukan kenan kuma sai Ummy ta dakata ta d'ago Hamna tace "Hamna ya kike so ayi? Wallahi bana son kowa yaji labarin nan, bayan b'acin rai da zan gani har da kunya, Hamna zanji kunya sosai ta iyayenki, ki amince da d'aya daga cikin zab'in nan Hamna." Cikin share hawaye tace "Ummy ina jin tsoro sosai wajen zubar dashi, idan wani abu ya faru sai kin fi ganin b'acin rai." "To kenan kin amince na zama uwar jikana?" Ummy ta fad'a tana mai kafeta da ido dan jiran amsarta, kallonta ita ma tayi tace "Amma taya haka zata faru Ummy?" Murmushi ta mata tace "Kin manta ni likita ce? Hamna inhar kin amince wannan ba matsala bane, zamanki gidan nan ne kawai zai bamu matsala." "Kamar yaya?" Ta sake fad'a kanta a matuk'ar d'aure, saida suka gyara tsayuwarsu da kyau sannan tace "Zan fad'awa kawunku ina da ciki, akwai tablet d'in da zan fara sha wanda zai sauya min yanayi na, daga yanzu har zuwa lokacin da cikinki zai shiga wata hud'u zaki zauna a gidan nan, amma fa sama da wannan lokacin ba k'aramar barazana bace garemu ki ci gaba da zama anan." Yamutsa fuska tayi alamar mamaki tace "To Ummy ina zan koma? Kinsan Hajia bata barinmu fita haka kawai, bare na koma wani wuri da zama, makarantar dana shiga ma ta koyon kwalliya da yaya na samu ta barni Ummy?" Dafa ta Ummy tayi tace "Yanzu dai mu fara da wannan, kafin tafiyar tayi nisa zamu san abunyi a gaba." Cikin raunin murya tace "Ummy ina jin tsoro, kar wani abu ya faru kuma a d'ora miki laifin komai." Murmushin yak'e ta mata tace "Karki damu, koma me zai faru zan d'auka, kuma in dai har zakiyi yanda nace miki to babu abinda zai faru da yardar Allah." A hankali ta jinjina kai tace "Shikenan Ummy, zanyi duk abinda kika fad'a min." Murmushi ta mata sosai tace "Yawwa yarinyata, yanzu da fari ki zama jaruma, duk abinda kika ji ki dinga k'ok'arin jurewa sannan kiyi gaggawar fad'a min, ko da baki jin dad'in jikinki ka da ki bari kowa ya sani idan ba ni ba, ni kuma yanzu zan bawa *Mamuda* (dreba) kud'i ya siyo min wani magani a pharmacie, idan kika karya kumallo sai ki sha." Jinjina kai ta sakeyi sannan Ummy ta jata suka koma ciki, kamar yanda ta fad'a bayan anyi karin kumallo ta bata magani tasha sannan suka tafi wurin wuni na biyu. Da magrib lokacin da ake shirya amare dan halarta wata walimar a lokacin kuma aka shirya aka tafi wankan angaye, kasancewar wankan farko ne dangin uwa ne sukeyi yasa Jibril yana b'angaren nashi uwa, Junaid ma haka sai kuma Ammar da Amar wanda suke gidan *Zulai* wacce yaya ce ga Sa'ada sai dai ba uwa d'aya ba haka kuma ba uba d'aya ba, dan ita duk danginta da suke ciki d'aya suna Agadez, Amar ya riga Ammar isa gidan sosai, dan har saida yayi nashi wankan ya fito sula tafi da nashi abokan Ammar bai zo ba, hakan yasa dangi suka fara fad'a da tsegumi suna fad'in Ammar ya raina mutane, wasu har sunyi shirin tafiyarsu suka ji rubdugun motoci kamar zasu fasa unguwar, a k'alla mota ma tafi guda ashirin, moto kam ko tunanin k'idayasu ma bakayi, (infa baku manta ba abokanshi ma manyan mutane ne wanda na b'oye sunan wasu kuma anan gaba zan canza sunan wasu saboda tsaro), tabbas abokai sun mishi kara tun anan, kuma dama Ammar mutum ne ruwa biyu, yana kyautata alak'arshi a waje ga kuma mutanen kirki, akasin haka kuma zakaji ba dad'i, magana dai ce zai iya fad'awa koma wanene kai kuma babu ruwanshi. Dangin sun fito waje dan ganewa idonsu amma abokan Ammar da yake akwai shak'iyai ciki kamar shi sai suka bud'awa Ammar hanya yana shiga cikin gidan suna mishi b'arin kud'i, kud'in ma sababbi kar dasu ko karyawa babu, (harkar fa ta manya ce), haka Ammar ya dinga ratsa kud'in nan wasu har takasu yake yana shiga cikin gidan, *gaba da gabanta*, sai gashi kama daga yara har uwayen suna bin bayan kud'in nan da suka ga in aka watsa ba'a komawa ta kansu suna wasoson d'auka, nan fa gidan ya hargitse da hayaniya ana ta ihu ana tsintsar kud'i, saida ya kai k'ofar ban d'akin da zai shiga wankan da taimakon jagorancin k'anwar Zulai sannan suka daina watsa kud'in, wani daga cikin abokan ne mai sunan *Pappa* ya kalli sauran yace "To mu jira shi ya fito sai mu d'ora ko." Haka kuwa akayi, k'anwar Zulai da su Husseina ne bakin k'ofar ban d'akin suna cewa "Ammar wallahi kayi wankan kirki karka zubar da ruwan nan ka fito." Ammar dake shirin cire dogon wandonshi jin haka yasa ya tsaya yana murmushin mugunta yace "Ya banyi tunanin haka ba? Shawara mai kyau." Tsaf ya mayar da kayanshi jikinshi, bai tsaya komai ba ya d'auki bokitin ruwan wanda shi kanshi sabo ne Zulai ta siya, sannan kayan had'in da aka had'a cikin ruwan masu yawan gaske da kyau, uwa uba turaruka da aka zuba ciki masu tsada da k'amshi, ba b'ata lokaci ya juye ruwan a k'asa suka tafi a banza sannan ya aje bokitin ya fito, sana jin bud'e k'ofar shi wasu mata biyu suka rangad'a uwar bud'a kai kace buzaye ne su na asali, suma abokan suna ganin haka suka sake matsowa, uku daga cikin abokan wanda kana ganin kayan jikinsu zaka san naira ta kwanta tare Pappa ne suka sake zaro kud'i a aljihu suka fara tarara mishi kamar ruwa, gud'ar da matan ne keyi kamar zugasu ne suke wajen zuba kud'in, ganin har zasu fita basu daina ba abun harya k'azamce yasa su Husseina suka taresu tace "Dan Allah yara ku daina zuba kud'in nan haka ya isa, angode muku Allah ya saka da alkairi." Wani mai cikar kamala da haiba ne a ciki yace "Hajia karki damu, Ammar namu ne, lokacin na mu bikin yayi fiye da abinda mukeyi yanzun, wannan ba komai bane." K'anwar Zulai ce tace "Duk da haka dai ai sai ku ragawa ranar bikin, tunda yanzu ne aka fara." Pappa ne yace "A'a tanti, mu a wurin mu shagalin bikin Ammar tun jiya aka fara shi, ranar biki ma a shirye muke zamuyi fiye da haka, kawai ku bamu hanya." Ai kuwa wucewa sukayi ba tare da sun daina ba, Ammar na shiga mota ya saki murmushi, dan ko ba komai yaji dad'in abinda Pappa ya fad'a, daga nan gida suka wuce, su tarar anata hidima kamar yau ne bikin, kafatanin ahalin Gaga babu wanda baya da ankon gallelen leshin da akayi, sai amare da aka ma shiga irin ta barebari (asalin mahaifiyarsu Suley), sunyi kyau sosai musamman ma Amna kayan sun karb'e ta haka ma kalar shud'i da sararin samaniya, hatta gyaren kan da aka musu irin na barebari ne wanda ya fito sosai ake ganinshi, nan abokan Ammar suka kutsa dashi d'akin shi suka sashi ya canza kaya zuwa chadda kalar ruwan samaniya sannan suka fito, filin taron suka kaishi inda suka d'auke su hotuna shi da amaryarshi, yau ma dai kamar jiya lafiya aka gama caskalewar aka kwanta kuma sai gobe idan gari ya waye a d'ora. Gida yayi shiru baka jin motsin kowa da komai, Ummy ce tasa lieutenant gaba sai rufe fuska take alamar ita kunya take ji, shi kam banda kallonta babu abinda yake yi har yace "Uwar yan biyu wai meye haka? ko dai kin tuna da k'uruciya ne?" Sake rufe fuska tayi da pilown dake hannunta tana murmushi, shima fad'ad'a murmushin yayi yace "Dan Allah ki fad'a min meke faruwa, ko kuma nayi hushi." D'agowa tayi da sauri ta kalleshi tace "Zan fad'a to." Zuro mata kunne yayi yace "To ina jinki." Saida ta sake rufe ido tace "Dama ai...dama, nayi b'atan wata ne, kuma n...na auna da kaina na tabbatar, cewa su Ammar zzza..su samu k'ane." "Me?" Lieutenant ya fad'a da k'arfi tana kallonta... *Alhamdulillah* *Yawan sharhi, yawan rubutu.* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` 💘💘💘💘💘💘💘💘💘 *A SANADIN K'AUNA* 💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘 _Barka my BK, ina tayaki murnar kammala wannan novel naki, Allah ubangiji ya baki ladan fad'akarwa, Allah ya saka miki da alkairinsa, kurakuren da kikayi a ciki ya yafe miki, sai mun jiki a next novel idan Allah ya amince._ _Bismillahir rahamanir rahim_ _33_ Baki har kunne lieutenant yace "Uwar yan biyu da gaske kike fad'a min maganar nan kuwa?" Kallonshi tayi tace "Da gaske mana, muna irin wannan wasar ne?" Girgiza kai yayi yace "A'a." Kallon gefe yayi yace "Kai amma wannan abu sa mamaki da kuma d'aure kai." Kallonta yayi yace "Wato ke idan na fahimceki irin haihuwar rak'uma kikeyi, kai Allah nagode maka abisa wannan kyautar." *Washe gari* da sassafe lieutenant ya fito cike da farin ciki da zumud'i, duk da yana jin nauyin fitowa kai tsaye ya fad'awa Hajia Sa'ada na da ciki, amma yayi niyyar fad'a mata ko da a birkice ne yanda zata gane ko da kuwa hakan na nufin yayi wani abu a aikace ne da zaisa ta fahimta, dan rashin fad'a mata da wuri zaisa yasa fad'a da tsegumi ranar da cikin ya bayyana. Yana isowa falonta saiya samu Zeituna kwance akan kujera da alamar galabaita a tare da ita, da sauri ya k'arasa ganin babu Hajia a wurin, yana zuwa ya zauna ya kamta ta tashi zaune yana kallonta yace "Zeituna lafiya? Me yake damunki ne? Me kike yi anan kwance?" Saida ta k'ara yamutsa fuska tace "Bana jin dad'i ne, ko baccin kirki banyi ba saboda amai." Cike da nuna kulawa hankali a tashe yace "Subhananallah! Amma kuma shine baki fad'a min ba kika ja baki kikayi shiru, to tashi mu tafi asibiti a duba ki." Kallonshi tayi tace "Duk likitocin da muke da su a gidan nan sai mun tafi asibiti?" D'an dafe kai yayi tare da tashi tsaye yace "Wallahi na sha'afa, bari na wa Sa'ada magana saita duba ki." D'akin Ummy ya nufa da rawar k'afa, zai shiga Hajia ta fito daga nata d'akin, ido hud'u da sukayi ya sashi tsayawa ya sunkuya yace "Ina kwana Hajia." Saida ta harareshi sama da k'asa tace "Meye kuma na wannan rawar k'afar zaka shiga d'akin ta? Ina ce ga amaryar can ka baro a falo, Hassan anya kuwa baka zama lusarin namiji ba." Cike da ladabi yace "Yi hak'uri Hajia, dama yarinyar can ce bata da lafiya, shine zan kira Sa'ada ta dubata." Kallon Zeituna tayi ta kuma kalleshi tace "To sai me? Nace sai akayi yaya? Akan bata da lafiya ne kake wannan saurin kamar zaka tashi sama?" Dogon tsaki taja kafin tace "Meke damunta? Nasan dai ba zai wuce tace ciki ne da ita ba ko? To kayi farin ciki zaka sake zama uba a wannan shekarun naka." Lieutenant da yake jin kamar yayi kuka jin abinda ta fad'a yasa ranshi sanyi, idan Zeituna ma ciki ne da ita shi kam Alhamdulillah, mata biyu a lokaci d'aya zasu sake haifa min yara, watak'ila ma a cikinsu wata ta haifi yan biyu, tunanin hakane yasa shi sakin murmushi, yana ganin Hajia ta nufi falon ya biyo bayanta, tana zuwa ta zauna tana k'arewa Zeituna kallo, fuska a had'e tace "Kinyi farin ciki ko? Hankalinki saiya kwanta tunda gashi kin nuna min kun gyauraya ke da Hassan har zaki haihu dashi kema." K'asa tayi da kanta tana wanda da yatsun hannunta, tana so ta tashi ta koma d'akin ta sai dai tana jin tsoro, lieutenant da farin ciki ya gama baibayeshi ne ya kalli Hajia yace " Hajia ai ita kanta Sa'ada bata da lafiya." Wani kallo ta watso mishi mai kama dana k'yama tana cewa "Ban gane bata da lafiya? Meya sameta ita kuma?" Shiru yayi haka ita ma kallonshi take tana jiran amsa, fahimta da tayi yasa ta canza yanayin kallon da take masa tace "Me kake nufi? Hassan wai ita ma Sa'ada ciki ne da ita kake so kace?" Sunkuyar da kai yayi baice komai ba wanda yayi daidai da fitowar Ummy daga madafa, k'ura mata ido tayi tana kallo harta k'araso kusansu, babu wani abinda ya sauya a jikinta, dama ita d'in jawur yake kuma ba k'iba ce da ita ba, idan da akwai abinda za tace ta mata bai wuce tace ta d'an rame ba, saida Ummy ta gaishe da Hajia da lieutenant tare da bashi kofin shayin dake hannunta, ta juya zata koma ga aikinsu kenan Hajia tace "Sa'ada, wai ciki kika ce mishi kina da?" Wata irin kunya ce ta rufe Ummy tare da fad'uwar gaba, shiru tayi ba tace komai ba sai zazzare ido take, Hajia na ganin haka cikin hushi tace "Amma dai ke akwai jahila, yanzu Sa'ada da girmanki ne zaki wani d'auki ciki? Shekararki nawa rabonki da ki haihu? Har an fidda rai da sake samun haihuwa daga gareki sai kawai yanzu ki wani ce kina da ciki, anya kuwa dan Allah ne kika yarda kika samu cikin nan, kenan dama can kina haihuwar kawai iskanci ne yasa sai lokacin da kika yi niyya kike yinta, ko kuma dai dan kinga kishiyarki na da ciki ne kema kika d'auka?" Tsaki Hajia tayi tare da mik'ewa ta bar falon zuwa farfajiyar gidan, Ummy da kanta ke k'asa saida taga fitarta ta d'ago a hankali ta sauke ido akan Zeituna, ido hud'u sukayi dukansu hawaye ne suke, da sauri Ummy ta juya ta shiga d'akin ta tana kuka, ita ma Zeituna fashewa tayi da kuka wanda yasa lieutenant rasa yanda zaiyi, kallonta kawai yake bai iya cewa tayi shiru ba, dan shi kanshi abinda Hajia ta mishi ji yake kamar yayi kukan, dan har yanzu baiga dalilin da zaisa mahaifiyarshi ta dinga tozartashi irin haka haba ba har a gaban matanshi. Ammar ne ya shigo falon cikin shiri da alamar fita zaiyi rik'e da leda a hannunshi, ba tare da lieutenant ya san da zuwanshi ba ya tsaya bayanshi yana kallon Zeituna dake zubar da hawaye, cike da nuna damuwarshi a kanta yace "Uwa lafiya? Meya faru kike kuka?" A d'an tsorace lieutenant ya juyo dan baiyi tsammanin mutum a bayanshi ba, ganin Ammar yasa yayi tsaki cikin jin haushi yace "Kai wane irin sakarai ne? Sai yaushe ne zaka fara sallama idan ka shigo wuri? Dubi yanda ka tsorata ni dan Allah." Ko kallon inda yake baiyi ba yace "Dama a tsoracen kake shiyasa, meya samu uwata nake so na sani har take kuka?" Mik'ewa yayi tsaye yace "Idan an fad'a maka me zakayi? Zak..." Bai k'arasa ba Zeituna ta d'ago kai ta kalleshi tace "Dan Allah Abban Ammar." Kallonta yayi ita kuma ta dinga lumshe mishi manyan idonta masu yalwar gashi, juyawa yayi ya fice a fusace daga falon, matsowa yayi kusanta yace "Uwa me aka miki kike kuka?" Girgiza kai tayi tace "Ba komai, bana jin dad'i ne." Murmushin ba gaskiya bane ya mata yace "Uwa ko dai Hajia ce ta b'ata miki rai?" Kallonshi tayi da alamar tambaya a fuskarta, lura da hakan yasa yace "Eh mana, ita ce dai mai d'ab'iar b'atawa kowa." Murmushi tayi tace "Ba komai." Tab'e baki yayi ya mik'o mata ledar yace "Ki bawa Amna wannan." Har ya juya zai fita Zeituna tace "Ba zaka shiga kaga Ummy ba? Kamar tana cikin damuwa fa." Yana juyowa ya kalleta da alamar damuwa da tashin hankali yace "Meya sameta? Wani abun ya faru ne?" Girgiza mishi kai tayi hakan yasa ya mayar da akalarshi kan d'akin Ummy, yana ya tsaya bakin k'ofa, har ya d'aga hannu zai k'wank'wasa sai kuma ya tsaya, turawa kawai yayi ya shiga babu sallama sai dai babu kuzari a tare dashi, Ummy na fitowa daga ban d'aki ta wanko idonta ta ganshi tsaye, tunawa da cewa duk abubuwan nan da suka faru sanadinshi ne yasa Ummy jin haushi, aje k'aramin towel d'in hannunta tayi ta giftashi zata wuce ta bar d'akin, cikin taushin murya yace "Ummy me yake faruwa ne?" A zafafe tace "Ban sani ba, koma meke faruwa ai kai ne sila, dan haka ka fita idona in rufe wallahi kafin na sab'a maka kaima." A sukwane ta fice daga d'akin ta barshi tsaye, a kasalance ya juyo ya fita shima bai bi takan kowa ba, mai gadi na bud'e mishi k'ofa ya taka motar da k'arfi zai wuce, kamar an tsayar dashi kuma saiya taka birki da sauri wanda ya haddasa tashin k'ura a bayanshi, gidan dake manne da na su gidan ya k'urawa ido yana kallo, tabbas ada akwai mutane cikin gidan ya kuma samu labarin barinsu gidan, sai dai baisan waye ya siye gidan ba da yaga yanzu an mishi sabon gini, irin ginin da akama gidan ne ma ke bashi mamaki, alamu sun nuna babban gidane daga ciki, daga wajen kawai zai iya d'aukar hankalin mai kallo daga waje saboda wata kalar panti da aka shafa mishi mai kama da carreau (tiles), ga shukoki gajeru da suka k'awata k'ofar gidan sunyi luf-luf dasu gwanin kyau, hak'ik'a an kwana biyu da yaga ana ginin wurin, amma yanda aikin yayi sauri yana bashi mamaki, taka motar yayi ya wuce inda zashi. Tun bayan sallah la'asar dangi na kusa dana nesa suka hallaro, ranar ta yau kam babba ce dan haka ma takanas takano aka d'auko mawak'i daga Agadez, nan fa aka fara kid'in guitar (jita) ba kama hannun yaro, duka mutanen kowa na zaune kan manyan carpet d'in da aka shinfid'a tare da mangal da butocin shayi anata zugawa, wasu kuma a gefe suna gasa gurasa ana ci ana sha ana raha da nishad'i. Ana haka kuma bak'i suka fara zuwa daga garuruwa daban daban, zuwa sallah magriba gidan nan baya zaunuwa ga duk mai son shiru, dan kowa da nashi dangin da suka zo. Amare na d'aki cikin shiga ta buzaye inda aka lullub'e su ruf da turkud'i, sai bayan sallah isha'i aka fito dasu dan kowace nata angon ya hallara a wurin ana so su musu kari, haka aka shigo dasu tsakiyar filin inda aka ta kid'in guitar kamar zai tashi gidan, buzaye da suka san darajar abin sai b'arin kud'i sukewa mawak'in, amaren na zuwa aka jerasu gaban angayensu, har fuskarsu rufe take hakan yasa kowane ango ya fara nazarin ina tashi amaryar, dan kayan manya ne wanda suka sa basu wani banbantasu ba sosai, Ammar tuni ya hangi tashi dan dama duk ciki tafisu kumari da albarkatun jiji musamman mazaunai, Jibril dake tsaye kusanta ne ya ji Ammar ya janyoshi ya ajeshi gaban Jamila yana fad'in "Dan ubanka ina kai ina wannan kayan? Ai sai ni babban yayanku." Kallonshi Jibril yayi yana dariya ya mishi rad'a a kunne yace "Ni ma da zaran ta shigo hannu na zan mayar da ita manyan kayan ai." Mayar da kallonshi yayi kan Amna yace "Allah yasa kana da ingantacciyar madarar da zata zamar mata vitamin a jiki." Jibril fashewa yayi da dariya ya kai mishi duka a kafad'a yace "Gaban k'annan ka kake fa." K'ala baice ba sai fito da kud'i da yayi a aljihu, sabbi ne a mik'e suke kar wanda bla (2000) nasu ma mai kyau ne, mayar da d'aya hannunshi yayi ya goya a bayanshi d'ayan hannun kuma ya fara zuba mata kud'in, suma dai kowa ya fito da tashi suka fara zuba musu kud'in, saida kowa ya gama sannan aka mayar da amare d'aki su Ammar na fita wasu matasa suka shigo gidan suka ce an aikosu da sak'o yana waje, biyu daga cikin dangi ne suka fita wajen, suna zuwa suka samu wasu manya manyan shanu guda biyu, d'aya ta Ammar d'aya ta Amar, gud'a aka saka tare da shelantawa na cikin gida abinda suka bayar, shanu guda biyu daga angaye ayi sabgar gobe dasu, ana cikin wannan farin cikin jiniyar motoci ta karad'e unguwar, GVR Gambo ne ya zo tare da matarshi, ikon Allah aka ce wai sai kallo, kowa na wajen yasan Hajia da yauk'i da kamkamba da miskilanci da shan k'amshi, amma sai gashi yau sunga surukurta wacce ta taketa a komai, ba kowa take kallo ba kamar yanda ba kowa take amsa gaisuwarshi ba, bugu da k'ari tare take da wasu matasan mata biyu, wanda kowa na gidan ya samu labarin cewa d'aya wacce zata dinga mata girki ce, d'aya kuma matashiyar mai yi mata kwalliya ce ta musamman, hatta masauki na musamman da aka ware musu saida tasa suka gyara mata shi sannan ta kwanta, sai dai bata ji dad'in yanda Hajia da kuma babbar matar gidan wato Ummy suka k'i kwantar da kansu a wajenta ba, domin kuwa Ummy a sama sama suka gaisa dan halin da take ciki ma ya isheta, Hajia ma k'amshi tasha sosai ta hakimce saida taje ta gaisheta. Yau ma haka gama sabgar saidai har gari ya waye wasu basu kwanta ba, saboda anata gyaran kayan abincin da za'a girka da safe wanda za aci bayan d'aurin aure. *Weeding day* (💃💃💃💃💃💃💃) Da misalin k'arfe *08:30* na safe dubbanin mutane ne suka shaida d'aurin auren amare uku da angayensu a k'ofar gidan *Alhaji Suleymane Gaga*, sai auren Maryama da aka d'aura shi a gidan malam Rabi'u dake nan cikin garin, su Husseina duka sun halarci d'aurin auren, bayan an d'aura anata gaisawa har Alhaji ya nemi gabatarwa da malam Rabi'u k'annan shi Hassana da Husseina dan su gaisa, Husseina na daf da shiga mota Labaran zai jasu Alhaji ya dakatar dasu ta hanyar fad'in "Yan biyu ku gaisa da kakan yarinyar mana." Juyowa Husseina tayi da murmushi a fuskarta, ido cikin ido, ido hud'u sukayi da malam Rabi'u, kakkafewa idonta sukayi a kanshi ta kasa katab'us, da k'yar ta d'aga yatsarta ta nuna shi murya na rawa tace "Kkk...kai, Rabi'u." Duk da shekaru sunja kuma ta tsufa, amma babu abinda ya hanashi ganeta, sunkuyar da kai yayi da alamar rashin gaskiya tare da cire hular kanshi ya fara firfita da hannun babbar rigarshi, Alhaji ne ya kalleta yace "Husseina, kin sanshi ne dama?" Labaran dake cikin mota zaune fitowa yayi ya zo ya tsaya gabansu ya k'ura musu ido, ita ma duk'ar da kai tayi ta fashe da kuka, Labaran ne ya sake matsawa cikin tashin hankali yace "Hajia lafiya kike kuka? Meya faru?" Fad'awa tayi jikin Labaran hakan ya sashi shafata yana daddab'ata alamar rarrashi, Hassana ce ta sake cewa "Husseina wai meke faruwa?" Da k'yar malam Rabi'u ya d'ago cikin i'ina yace "Ee.h to..ina ga dai.. ko bata da lafiya ne?" D'agowa tayi ta kalleshi tace "Banda lafiya? Me zai hana ka fad'a musu abinda ya faru." Alhaji ne yace "Wai me yake faruwa ne? Ku fad'a mana." Cikin tsananta kuka ta kalli Alhaji tace Ba komai, kawai mu tafi." Labaran daya kafe malam da ido shi dama har yanzu al'amarin mutumin na gindayar dashi yace "Hajia daga ganin mutumin nan yanayinki ya canza, dan Allah ki fad'a mana ko da wani abu mana ko hankalinmu zai kwanta." Juyawa malam Rabi'u yayi da nufin barin wurin sai Labaran yace "Hajia ko dai wannan shine..." Shiru yayi bai k'arasa ba dan da k'arfi malam Rabi'u ya juyo yana kallonshi, ita ma Husseina kallonshi tayi, sai Hassana ce tace "Shine me?" Cike da ladabi yace "Hajia kwanan baya sanadiyar ganinshi yasa na miki tambaya akan mahaifina, jikina yana bani kamar akwai wani abu tsakanina da shi, kuma alak'ar zata iya zama mai k'arfin gaske, amma gudun b'acin ranki yasa bana iya aiwatar da komai." Duk shiru sukayi sai Husseina data share hawaye ta kalli Labaran tace "Tabbas shine, ba zan tab'a manta kamanninshi ba." Hassana da Alhaji ne suka ce "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." Alhaji ne ya d'ora da "Ya ilahi, malam Rabi'u?" Husseina shigewa tayi mota ba tare data kalli kowa ba, Hassana ma shiga tayi tana waigen malam, Labaran dake kallonshi rasa abinyi yayi, sai kawai ya juya shima ya shiga mota ya tayar, Alhaji ne yayi k'arfin halin matsawa kusa dashi yana kallon idonshi yace "... *Alhamdulillah* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _34_ "Gaskiya banyi tsammanin haka ba, sam abun baiyi min dad'i ba, cikar kamalarka tasa ban tab'a maka wannan zaton ba, tashin hankalin daka jefamu cikinshi Allah kad'ai yasan iyakarsa, amma yanzu a matsayinmu na manya ba zamu ce da kai bamu yafe maka ba, domin kuwa bayyana da kuma tonuwar lamarin nan a yanzu bayan tarin shekarun da aka kwashe ya isa yasa mu fahimci akwai wani al'amari mai girma, kuma gashi a bayyane auren *Maryama* da Junaid yayi, sai mu musu fatan alkairi." Yana gama fad'a ya wuce shima inda colonel da kanshi ya bud'e mishi mota ya shiga suka wuce. Husseina na zuwa gida d'akinta ta wuce ta dinga kuka, sam bata so had'uwar ta da shi ba, amma gashi yau ta gani, haka farin cikinta ya koma bak'in ciki, haka shima Labaran, kana ganinshi zaka gane yana cikin damuwa, sai dai shi har zuciya yana so ya gana da mahaifinshi, *uba*, wanda ya rasa tsawon shekaru, bai tab'a d'ora idonshi akan ko da dangin ubanshi ba bare uban. Kamar yanda baya b'oyewa Soueiba komai yanzun ma bai b'oye mata ba, ita kanta abun ya d'an dameta sai dai bai hanata karb'an duk wani daya zo gidan dominta ba. Tako kamar na gwiwa, d'aya bayan d'aya sai kace wata sarauniya, yayin da mai aikinta ke biye da ita a baya rik'e da jakarta, babbar riga ce jikinta mai kama da babbar rigar maza, d'aurin d'an kwalin ya hau kanta sosai, sai yalolon gyalen data d'ora a kafad'a d'aya da manyan waya har biyu a hannuwanta, zobuna da sark'a da yan kunnai duk gwal ne, dogayen takalma a k'afarta da suka dace da kalar kayan, da gani babu tambaya kasan mai yana aiki a wurin, jan nata har ya k'azamce ta yanda take d'aukar ido, ga kuma hodar data d'auka ta k'ara fito da ita, cike da k'asaita da jin kai da isa ta k'arasa tsakiyar filin da ake kad'in guitar. Yau a k'ofar gida ne ake kad'a guitar d'in sai tarin yan zaman biki da suka zagaye mawak'an suna kallon rawar da wasu maza keyi irin ta buzaye, bayan k'arar guitar haka wurin ya hargitse da shewa irin ta buzaye (ma Sajida nasan zaki fahimci irin shewar, 😂) wasu na karkad'a harshe abun birgewa ana rawa wacce tafi kama da tsalle tsalle, dan wani tsallen sai anyi k'asa sosai ake yin sama ana harba k'afafu 😂(abun birgewa). Zuwan *Aissata* yayi daidai da zuwansu Ammar shi da abokanshi wanda suka zo d'aukar abincin da yasa Zeituna ta girka mishi, zai shiga gidan Sayyada yar Fatime da kuma wasu daga cikin yan mata suka taho wurinshi, nan suka tilasta mishi sai sun d'auki hoto dashi, sun d'auki hoton zai shiga sai kuma ya kalli wurin taron, nan ya hangi Aissata ta bud'e bakin jaka tana watsa kud'i kamar hauka, murmushin zaki gane kurenki yayi mata ya nufeta, nan ya kutsa filin taron ya sameta yana murmushi yace "Uwarmu sannu da k'ok'ari." Kallonshi tayi a sama tace "Cava." Kallon mai bisa ruwa ya mata yace "Uwa irin wannan lik'i haka, kice dai aljihun uban namu yayi kuka yau?" A wani yamutse ta kalleshi tace "Qu'est ce que tu remarque (Me ka lura dashi)?" Murmushi ya mata yace "Eh to, da yake ai a lokacin aurenku da tonton munje Niamey, kuma har gidanku muje kafin ma d'aurin auren, in baki manta ba ai har d'akin Ummynki na shiga na ci abinci." Kallonshi tayi da alamar rashin fahimtar zancenshi ko d'aya, hakan yasa tace "De quoi tu parles? (Akan me kake magana), je ne comprends rien (Ban gane komai ba)." 😂 _Hyahyahya, bata gane komai ba, yana nufin ya ga gidanku ke d'in ba yar kowa bace bare ace zaki iya fantamawa da kud'in gidanku._ Murmushi ya mata ya k'urawa fuskarta ido yace "Amma uwarmu powder nan fa ta karb'i fuskarki, wallahi yanda kika san wata kyakyawar sarauniya." Dariya ya mata ya wuce cikin gidan, ganin babu isassar hanyar da zai wuce yasa shi tambayar *Farisa* k'anwar Jibril inda uwa Zeituna take, ita ta fad'a mishi suna gidan da za akai amare suna girki, da mamaki ya kalleta yace "Gidan da za akai amare? Wane gidan to? Bayan kowa da nashi gidan, Ina ne gidan?" Nuna mishi gidan nan tayi tace "Yah Ammar gaya nan, yanzu ma ana kai kayansu ne ana gyaran d'aki." Jim yayi alamar tunani, murmushi ya saki yace "Duk yanda akayi wannan aikin Alhaji ne, dan shine kad'ai yake matuk'ar son ya ga iyalinshi a wuri d'aya, baya son ganin sunyi nesa da juna, shiyasa duk da kowa na da hali amma suke manne gida d'aya." Kallon Farisa yayi yace "Je ki kira min ita." Galala ta kalleshi jin yace wai ta kira mishi ita, Zeituna fa yake nufi, wucewa tayi shi kuma ya fito dan ya jirata a waje, sai dai yana tunanin yanda zasuyi rayuwar aurensu a kusa da iyayensu, a gaskiya ya so ya bar gidan nan ko ya samu salama, amma kuma ba zai iya yi wa Alhaji musu ba, yana cikin tunanin nan Zeituna ta fito cikin shirinta sai dai duk ta had'a gumi saboda aikin da suke, girki ya tambayeta tace an ida dan haka yasa aka fito da manyan kuloli aka zuba musu, su Amar na zaune a k'ofar gida suma suna nasu casun, sai dai ko magana bata had'a shi da ko d'aya daga cikinsu ba, sai Junaid wanda tuni wasu daga cikin dangin Alhaji da kuma dangin Soueiba suka tafi d'aukar amaryarshi Goûré tare da abokanshi. Hajia ce tsaye a d'akin Alhaji ta tisashi gaba tana fad'in "Akan mene zaka musu gini ba tare dana sani ba? Sai yanzu kawai ana maganar gyaran d'akin sai ka wani ce wai ga gidansu nan, sun fad'a maka suna sha'awar zama anan d'in ne?" Shiru Alhaji ya mata kamar bai jin me take cewa sai jan carbin hannunsa da yake, d'orawa tayi da "Babu wanda baya da lafiyayyen gida a cikinsu, an musu wannan tanadin ba tun yau ba saboda irin wannan ranar, kuma kai ma kasan da haka, amma ka had'e musu gida d'aya su hud'u, kuma wannan kurkukun gidan me zai musu? Sai kace wasu jarirai ne su da ba zasu iya kula da kansu ba saida taimakonmu, to ni gaskiya wannan gidan bai min ba, inhar kana son su zauna kusa da kai ne to sai dai in zaka raba musu gidan ko da hakan na nufin ka siye duk rabin unguwar nan ne." A hankali cike da dattako ya d'ago kai ya kalleta, hak'ik'a shi d'an halak ne, kuma har yanzu yana tuna hallacin mahaifinta gareshi, wanda kusan shine silar arzik'in shi, ya mishi hallaci sosai a rayuwa, dan haka har yanzu yake iya shanye duk wani wulak'anci da k'ask'anci daga wajenta. Murmushi ya sakar mata tare da mayar da kanshi ya sunkuyar, hakan kuma k'ara b'ata mata rai yayi, cikin hassala tace "Wato ga mahaukaciya ko? Shikenan ba komai, yanzu fad'a min ita kuma waccen k'ofar da naga ana yi ta kusa da b'angaren samari ta mecece?" Ba tare daya kalleta ba yace "K'ofar da zasu dinga shigowa kai tsaye ba sai sun shigo ta waje ba." "Amma w..." Kallon daya mata yasa taji ta kasa k'arasawa, ita kanta tasan a cikin zamantakewarsu akwai ragowa da d'aga k'afa, ta kuma san yana k'yaleta ne kawai saboda mahaifinta, amma ba dan haka ba ko a zahiri tasan yafi k'arfin zama lusari a gidanshi, turo mishi d'an k'aramin bakinta tayi mai kama dana Ammar tare da jujjuyashi ta fice da sauri, murmusawa yayi tare da girgiza kai yace "Allah ya shiryaki Zeeya'atu, ina fatan ganin ranar nan." Duk da a k'afa aka shigar da amare d'akunansu, amma hakan bai hana abokanan angayen yin kururuwa ba a k'ofar gidan kan ababen hawansu, saida suka tayar da k'ura sukayi juyi da motoci, Maryama ma sun iso lafiya ta shiga d'akin ta. B'angare hud'u ne a cikin gidan wanda daga waje ake mishi kallon k'arami, kowane b'angare matsakaicin doron zabuwa 😂 ce aka mishi, a kowane b'angare kuma yana d'auke da falo da d'aki uku a ciki sai k'ananun madafa (cuisine), a kowane d'aki kuma akwai ban d'aki a ciki bayan wasu ban d'akin dake akwai guda biyu a waje, idan ka cire Maryama da ita ma babu laifi an mata kayan d'aki, duka amaren saida aka cika dak'unan da kaya, Gambo da Labaran ne sukayi wannan k'ok'ari bayan doguwar musu da akayi, Labaran yace shi ya d'auka zaiyi musu kayan d'aki, colonel yace shi zaiyi, lieutenant ma haka, a k'arshe dai Gambo da Labaran suka barma, babu ce kawai babu a d'akin su, hatta kayan kallo basu bari ba saida suka zuba musu, kuma kayan duk sanfiri d'aya ne kala da abinda ba'a rasa bane ya banbanta. *Party* Kayan da Ammar ya d'inka mata ne ta saka, leshe ne da ak'alla kud'in zasu ishi wani talakan rayuwa na tsawon watanni, kalar ruwan madara ne da bleue wanda ya k'ona sosai, haka shi shi ma tanffatsetsen yadin dake jikinshi kalarsa take, mota dai ba wata tsiya ba kam kamar suyi magana, dan wajen ajiye motoci a babban hall d'in ma kasa d'auka yayi, duk girman gurin saida aka matsu akayita had'a gumi, har ya zama ba'a jin tashin kid'an dake wurin sai jininin mutane da kuma hayaniyarsu. Da gani kasan babban biki ne na manyan mutane kuma masu tarin dangi, kowa daka gani shafar gumi yake saboda matsatsi yayi yawa, abincin kam dama ko da colonel ya samu labarin jama'ar dake wurin ya sake odar abincin a restaurent har guda biyu, da hakane aka samu abinci ya wadata a wurin, duk wanda bai samu ba to baya kusa sanda aka raba. Hasken waya kam ta ko ina ganinshi kake ana d'aukar hoto, ana cikin wannan rak'ashewa aka ce Hamna ta zo a d'auki hoto kuma a dole su sa Ammar tsakiya. Hamna na tsayawa ta wurga masa harara tana gunguni k'asa k'asa, Ammar dake amsa waya cikin akasi idonshi suka sauka kanta tana harararsa, kashe wayar yayi ya murtuke fuska yace "Ke uban wa kike harara? Allah kankana ki kiyayeni." Murgud'a masa baki tayi tace "Ank'i a kiyayeka, da wani abu da zakayi ne?" Kallonta yayi da mamaki yace "Kutumar uba, ke ni kike fad'awa haka? Me..." Bai k'arasa ba ya juya ya kalli Amna dake ta doka murmushi, murmushin ya mata shima yace "Amaryar, ci gaba da murmushi irin haka kinji, bari na gama da kankana." Bai jira amsarta ba ya sake juyowa kan Hamna ya zaro mata ido ya sassauta murya yace "A waccen ranar me kika gani? Ga dukkan alama kankana ban baki tsoro ba, dan dana tsorata ki da ko ganina kikayi sai gabanki ya fad'i, amma akwai lokaci." K'wafa yayi ya juya gabanshi ita kuma tace "Tabbas." Da sauri ya juyo ya kalleta, d'orawa tayi ba tare data kalleshi ba tace "Tabbas akwai lokacin da zan huce haushina a kan ka, kuma tsoro da kake magana, kai a wa zanji tsoronka? Fasik'in? To ai ko abinda ya faru ma ni baisa na kalleka a matsayin namiji ba, watak'ila baka gama k'wari bane ko kuma dai kana da k'arancin lafiya, amma dai ka sani ni banji komai." Ruf ya rintse idonshi, yawu ya had'e masu d'acin gaske wanda suka sanya mak'walaton dake wuyanshi yin sama da k'asa, bud'a idonshi yayi wanda suka fara d'aukar launin ja, ya kasa d'auke idonshi a kanta saboda so yake ya tattartsa mata mari, amma ya rasa yanda akayi ya kasa d'aga hannun, ya tabbatar da wata ce ko Amna tuni data dafe kunci, to amma me yasa ita ya kasa. A hankali ya sake lumshe ido ya bud'e a kanta, tattaro kuzarinshi yayi yace "Da bana da lafiya da bakiyi kururuwa ba, da ban cika namiji ba da tafiyarki bata canza ba, yanzu kuma zan tabbatar da abinda kika fad'a ne idan har kika ga al'adarki a wannan watan." Wata mummunan fad'uwa gaban Hamna yayi, kallonshi tayi tsoro ya bayyana a tare da ita, fahimtar haka da yayi yasa ya murmusa ya kalli gabanshi yace "Ba alfahari nake ba, amma inada tabbacin ke bakiyi k'osawar da har madara zata kasa zama d'an mutum a cikinki da zubawar farko ba, musamman ni da nasan na zubata a daidai a lokacin da komai ke bud'e yana maraba da kowane bak'o ya shigo." Hamna kam fashewa tayi da kuka ta taka zata bar wurin tana fad'in "Allah ya isa, Allah saiya saka min, mugu azzalumi." Dariya yayi wacce ta fito da kyawunshi murya k'asa k'asa yace "Ba farau ke da zafi ba dama, ramau, kuma nima Allah ya isa da kika rabani da samartaka ta, muguwar kankana kawai." Amna dai da babu abinda take ji kallonshi kawai tayi, suna had'a ido ya sakar mata murmushi yace "Ina k'aunar ki amaryata." Kunya ce ta rufeta ta sunkuyar da kai, shi kuma kallonta yayi ya tambayi kanshi "Da gaske *kana k'aunarta*?" D'an murgud'a baki yayi yace "Ko bana sonta ai ina k'aunar ta, kuma yanzu matata ce sannan zata zama uwar 'ya'yana insha Allah." Tsam yayi sai alamar tashin hankali daya ziyarceshi lokaci d'aya, abinda ya fad'a mata ne ya dawo kanshi, *yanzu kuma zan tabbatar da abinda kika fad'a ne idan har kika ga al'adarki a wannan watan*! Tashin hankali, to idan fa haka ta faru? Wata zuciyar ce tace mishi "Haka ma ba zai faru ba, ai ka fad'a mata ne kawai dan ita ma taji zafi kamar yanda ta cizgaka." D'aga kafad'a yayi alamar ko oho sannan aka ci gaba da sha'ani, sai dai har aka tashi daga taron bai sake ganin Hamna ba, wanda hakan ba k'aramin dad'i ya masa ba, dan dama ganinta cikin shigar nan data fito da komai nata yana tayar masa da hankali, sai yaga duk idon kowa a kanta yake. Nan aka koma gida aka raka kowace amarya ta sake shiga d'akinta. Duk abinda aka saka ma rana dai k'ararre ne dama, sai gashi anyi an gama kowa ya kama gabanshi an bar amare da angaye da halinsu. *12:00* da sallama Jibril ya shigo d'akin da ledoji a hannunshi, Jamila dake zaune tsakiyar gadon kasa amsawa tayi dan gabanta ne taji ya tsananta fad'uwa, har saida ya zauna kusanta bata motsa ba, ganin bata da niyyar magana yasa ya aje ledojin hannunshi ya yaye mayafin nata yana kallon fuskarta, ajiyar zuciya ya sauke ya d'anyi k'asa da kanshi sannan yace "Jamila." Saida ta had'e yawu yafi sau biyar kafin ta amsa k'asan mak'oshi da "Na'am." Murmushi yayi jin firgici a cikin muryarta yace "Muje muyi alwala ko." Jinjina kai kawai tayi alamar to sannan ta sauko a hankali ta fad'a ban d'aki, yana zaune yana jiranta har ta fito, saida ya k'urawa fuskarta ido ganin ta wanke kwalliyar dake fuskar, mik'ewa yayi shima ya shiga, ba jimawa ya fito ya samu ta shinfid'a sallaya, gaba ya tsaya ita kuma daga gefenshi a baya suka kabbara sallah. A wajensu Junaid ma hakance ta kasance, bayan sun idar da sallah zai janyo ledojin shi yaga ta mik'e, da mamaki yace "Zauna mana, zo ki cika cikinki Hajia ta." Kallonshi tayi tace "Ina zuwa, zan canza kaya ne." A gabanshi, yana kallo ta zage rigarta ya rage sai bras a jikinta a k'arshe ma bras d'in cireta tayi ta saka ta bacci sannan ta janye siket d'in ta, yana kallo ta cire pant d'in ta ta saka na rigar baccin, juyowa tayi ta zo ta zauna kusa da shi cikin jijjiga jiki irin na yan duniya, nan suka fara cin kazar yana bata a baki ita ma tana bashi, tun basu ida ba wasan ya sauya ya kuma girmama suka haura kan gadon mulki. Amar ma har har sukayi sallah suka ci abinci idonsu bai had'u ba, har zuciyarshi baya son Umaimah so na soyayya, amma babu yanda zaiyi duk da yana da halin da zai iya ce ma Hajia bai sonta kuma ta amince, amma yayi hakanne saboda yan uwanshi. Yanzun haka kayan bacci ne ya sanya a d'akin shi ya dawo d'akin, tsaye ya sameta ita ma tayi shirin baccinta, k'ala bai ce mata ba ya haye gado ya kwanta, tana ganin haka ta kashe wutar d'akin ta d'auko bargo a ledarshi ta cire ta shinfid'a k'asa, ta d'auko matashin kai zata koma ya tashi zaune yana kallonta, cike da halin ko in kula yace "Kinga dawo nan ki kwanta, meye na kwanciya a k'asan kuma bayan ga gado?" Sam bata ji dad'in yanda ya mata magana ba, haka ta taso ta d'an zauna amma bata kwanta ba, shi ma daya kwanta baccin kasa d'aukar shi yayi yana kallonta, ganin haka ba zata gyara su ba yasa shi zura mata hannunshi alamar ta taho yace "Zo k'anwata." Kallonshi tayi ta kalli hannun, saida ta sunkuyar da kai sannan ta mik'a mishi hannun, jawota yayi ta matso kusa dashi ya rumgumota a jikinshi, d'aya hannun yasa yana shafa kumatunta a hankali, a haka haka kuma sai bacci yayi gaba da ita, a hankali ya gyara mata kwanciyarta ya ja mata lallausan bargon dake kan gadon sannan shima ya kwanta. A b'angaren *babban yaya* kuma nashi salon daban yake dana kowa, domin kuwa yana shigo ya hangeta tsakiyar gado ta nad'e k'afafu, tsaye yayi ya aje ledojinshi k'asa yace "... 😛 *Alhamdulillah* _Idan naga ruwan comment zakuji wani insha Allah._ 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _35_ "Amarya haka ake tarban miji?" Wani fad'uwar gaba taji, amma sai tayi shiru bata d'ago ba, takowa yayi saida ya tsaya kanta ya janye mayafin fuskarta, tallabo hab'arta yayi ya saka idonta cikin nashi, murmushi ya mata yace "Ai na d'auka kuka ne kike? Dana tambayeki kuka me kike?" Sunkuyar da kanta tayi tana k'ok'arin mayar da mayafin sai kuma yace "Kinga ta so ki gani." Hannayenta ya kamo ta sauko daga kan gadon suna fuskantar juna, tsaye k'ik'am ya mata yace "Taimaka min na cire wannan kayan, kinsan fa ban saba saka irin wannan kayan ba, kawai dai dan yana bikina ne ina so na fito a angona." Kasa kallonshi tayi sai kallon k'asa da take tana shafa wuyanta da tafin hannunta, ita fa wannan tijarar tashi ce tasa take shakkar aurenshi, ya zai ce ta taimaka mishi ya cire kaya? Ba ma zai barta ta mori amarcin ba wannan, kafeta yayi da ido yace "Ke dake fa nake." Da sauri ta kalleshi cikin tsoro ta zura hannu saman kanshi ta d'auke mishi hular, ajeta tayi kan gado ta kalleshi kamar zata fashe da kuka tana aika mishi da kallon dan Allah ka k'yale ni haka, hannu ya d'aga kamar zai mareta yana fad'in "Dallah ni kar ki min kuka, mage kawai." Ja baya tayi har ta fad'a kan gadon zaune tana binshi da kallo, cire babbar rigar yayi ya cilla mata ya rufe mata fuska, janye rigar tayi ta hangeshi ya shiga ban d'aki, k'amshin rigar daya daketa ne yasa ta k'ara mannata a hanci tana shak'a tana lumshe ido, tunaninta yanda zata iya wannan bahagon yayan nata take, wani k'asaitaccen murmushi ta saki saboda ganin sam bai b'ata nuna mata k'iyayya ba, tana cikin sakin murmushin nan ya fito ba tare data sani ba dan bai rufe k'ofar duka ba lokacin daya shiga, yana sauke ido a kanta yace "Jikanyar Hajia har na fara kasheki ne? To ai baki ga komai ba, sai ma anjima ko?" Kamar wata marar gaskiya haka ta lallab'a ta aje mishi rigar bata yarda sun had'a ido ba, matsowa yayi ya kama hannunta ta mik'e tsaye ya turata gaba yace "Je kiyi alwala ki zo muyi sallah, tunda ke ma kina da tsarki yau kwana zamuyi muna ibada." Juyowa tayi ta kalleshi baki bud'e, ta fara tsoratada al'amarin nashi kam, wani dolon murmushi ya mata yace "Yi sauri mana, ko so kike saina fara nuna miki komai a fili." K'ara k'ank'ance k'aramin bakinta tayi ta juya kamar wacce k'wai ya fashe ma cikin ciki, kamar a mafarki sai ji tayi an mareta a mazaunai, juyowa tayi da k'arfi ta kalleshi, kashe mata ido yayi yana d'an cije leb'en k'asa, da sauri ta sake juyawa ta shige ban d'aki, had'e fuska yayi kamar ba shine ke dariyar nan ba ya juyo ya d'auki sallaya yana shinfid'awa yana fad'in "Kaji min yarinya, ku mata kun d'auka ku kad'ai kuka iya kwarkwasa ko, to ni ma da nayi niyya dana zama karawi." Duk da ta gama alwalar amma saita kasa fitowa tana tunanin abinda zata tarar, ganin shiru yasa shi sanyo kai cikin ban d'akin, had'a ido sukayi tana tsaye gaban madubi ta jinjina a bango, ba tare daya shiga ba ya zura hannunshi ya kamota suka fito, suna zuwa ta samu hijabi ta saka suka kabbara sallah, suna kammalawa daga nan ya juyo ya fuskanceta, hannunshi ya zura ya d'an janye hijabinta daga kanta ya dafa kan nata ya karanta mata addu'a "Allahumma ini as'alukha khairuha wa khairu ba jabaltaha alaihi, wa a'uzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi." D'auke hannun yayi ya k'ara gyara zama ya k'ura mata ido yace "Amna, yau gani ni dake a d'aki d'aya a matsayin mata da miji, wannan wani al'amari ne daga ubangiji, domin kuwa a rayuwata ban tab'a tunanin zaki zama matata ba, sai dai ina farin ciki da kasancewarki matata d'in, dan zan iya cewa ko Ummy data raineku bata kaini saninku ba, yarinyar kirki ce ke, dan haka ina fatan Allah ya bamu zaman lafiya." Cikin sanyanyar murya tace "Ameen." K'arawa yayi da cewa "Amna, nasan kuna zuwa islamiyya, zan iya sanin zurfin karatunki?" Ba tare da sun had'a ido ba ta fara mishi bayanin matakin karatunta, kallonta yayi yace "Amma me yasa baki fara karanta arba'una hadisi ba har ki fahimce shi sannan ki fara bulugul maram? Duk littafin hadisin da zaki karanta idan baki karantashi ba ba zaki fahimci abubuwa dayawa ba, domin kuwa wasu malaman sunce gaba d'aya kafatanin musuluncin yana dunk'ule ne a cikin hadisai k'waya talatin, kuma wad'annan hadisan guda talatin suna cikin littafin arba'una hadisi, yayin da wani malamin shi kuma yace ai gaba d'aya addinin ma yana cikin hadisi guda d'aya ne tak, kuma wannan hadisin shima yana cikin littafin, kinga kenan indai har kina so ki fahimta zaifi miki ki fara dashi, idan kikayi nasarar kammalashi saiki fara da muwadd'a, kin gane?" A hankali ta jinjina kai alamar eh, mik'ewa yayi tsaye yace "Ki d'auko ledar ce ki juye abin ciki a faranti." Mik'ewa tayi ita ma ta d'auko ledar shi kuma taga ya fita, ita ma fitowa tayi inda ta tabbatar nan ne madafa ta shiga, d'auko faranti tayi da cup biyu ta dawo, har ta juye ta zuba komai shiru bai dawo ba, bakin gado ta zauna tana jiran ya shigo taji yanda zasu k'are dashi, ai kuwa yana shigowa ta kalleshi lokaci d'aya ta sauke idonta k'asa, farin dogon wando ne jikinshi na zallar kad'a da farar singlet, saida ya aje wayarshi a hannu ya k'araso yana fad'in "Wai ke me kike nufi? Kunya ce kike ji? Ina ce dai tare muka rayu gidan nan, kin sanni tun lokacin ina yawo da gajeran wando, haka nima na sanki tun ina saka miki wando da kaina, to kuma miye na wannan nok'ewar, dallah tashi ki canza kaya ki zo ki ci abinci cikinki yayi nauyi, idan ba so kike ki b'ata min rai ba yanzu na karya miki k'afafu." Tashi tayi da sauri ta nufi wajen kaya ta kuma nufa ban d'aki, ganin duk ta diririce yasa ya kama hannunta har ban d'aki, gashi dai sun shigo kuma babu alamar zai fita, cire mata hijabin jikinta yayi da d'an kwali ya jefosu kan gado dan bai rufe k'ofar ba, juyata yayi ya kama zip d'in rigarta ya cire, sake juyota yayi ya kama rigar zai zageta ta k'asa, da sauri ta d'an rik'e rigar tana kallonshi a tsorace, kallonta yayi gira a had'e yace "Meye? Amna kina so na ci uwaki ne a daren nan?" A hankali ta girgiza masa kai idonta har sun cika da k'walla, ko a jikinshi sai ma kama rigar da yayi ya zuge mata ita ta k'asa, sunkuyawa yayi ya fitar da rigar daga k'afafun ta ya d'ago, Amna da tuni tasa hannayenta ta rufe jikinta ta rintse ido, kamar daga sama taji yace "Wow, 'yar k'anwata ce ta zama haka? Lallai kun girma, gobe dole naje na yiwa kakarku godiya, domin kuwa ta min zab'in daya dace dani, kamar tasan irin yanda nake son matata ta kasance." Sunkuyar da kanta ta sake yi shi kuma bai kula ma da tsiyar da take ba, rumgume hannayen shi yayi a k'irji yana k'are mata kallo, duk da ta rufe abubuwa dayawa amma bai hana shi gane wasu abubuwan ba shima, fad'in k'ugunta da cikinta yasa mazaunanta suka zama masu d'aukar hankali, fuskarta ya koma kallo d'an k'aramin bakinta da kurmin idonta, wata tausassan dariya yayi a daidai lokacin Amna ta gaji da yin shiru ta bud'a ido a hankali, suna had'a ido ta sake rufe ido ta juya baya, hakanne ya bashi damar kallon kayan da suke d'aukar hankalinshi, jefo rigar yayi bata ko sauka akan gadon ba, rumgume ta yayi ta baya yasa hannun dama yana shafa mazaunanta, har ga Allah inhar zai fad'i gaskiya a lokacin daya ruk'unk'umeta saida yaji yanda jikinta ke rawa, amma kuma tsikar jikinta duk ta tashi, dan kar ya saba mata da tsoronshi yasa ya taushe abinda yake ji a lokacin, sakinta yayi yace "Maza kiyi wankan ki fito ina jiranki." Bata iya cewa komai ba saida taji ya rufo mata k'ofar, ajiyar zuciya ta sauke idonta na zubo da hawayen da suka mak'ale, da k'yar ta iya wanka ta fito, nan ma ta sameshi kwance akan gadon kamar jiranta yake, saukowa yayi ya bud'a wajen kayanta ya shiga bincika, wata riga ya samu iya gwiwa tsayinta fara k'al tare da wandonta a jikin rigar, d'aukowa yayi ya juyo gareta tana zaune tana shafa mai ya rufe robar man yace "Kina shafawa ne saboda jikinyi kiyi tsantsi na kasa kama ki da kyau, muguwa." Ita dai k'ala ba tace ba sai turare daya d'auka yana ta fesa mata har saman kai da bayanta saida ya feshe, mik'ar da ita yayi tsaye ya cire wandon daga rigar ya durk'usa k'asa irin dai yanda ake wa yara in za'a saka musu wando, k'in d'aga k'afar tayi hakan yasa shi d'agowa ya kalleta, cikin razananiyyar muryarta tace "Dan Allah yah Ammar." "Dan Allah me?" Ya fad'a ba tare daya daina kallonta ba, sake marairaicewa tayi tace "Zan saka da kaina, kayi hak'uri." Tsaki yayi yace "Malama d'aga min k'afar ki kafin na tsagaki gida biy..." Tun bai k'arasa fad'a ba ta d'an d'aga k'afa a hankali ta zura, kasa d'aga d'aya k'afar tayi ta fashe da kukan shagwab'a tace "Dan Allah yah Ammar ka barni zan saka, wallahi ni..." Tsaye ya mik'e yace "Ke me?" Bayan hannu tasa tana murza ido tace "Kunya nake ji wallahi." "Kunya?" Ya fad'a da k'arfi, ta hudar yatsunta taga yana k'ok'arin kwance d'aurin zariyar wandonshi yana fad'in "To bari na tub'e nima ki ganni sai ki daina jin kunyar, kinga kenan anyi 1-1." Da saurin bala'i ta sunkuya ta rik'e hannayenshi tana fad'in "Yi hak'uri yah Ammar dan Allah, ba sai ka cire ba." Kallonta yayi ya tab'e baki inda ta k'urawa fuskarshi ido, tunani take wai haka kowane ango keyi a daren farkonsa? Ko kuma ita ce amaryar da tayi wannan rashin sa'ar? Ita kam da zai barta ta kwanta ta huta da taji dad'i, amma bata ga alamar hakan ba a tare dashi, yana cikin d'aurawa yaga irin kallon da take masa, ba tare da sanin abinda take tunani ba yace "Tunani kike wannan wane irin daren farko ne?" Girgiza kai tayi ta sunkuya cike da dubara ta saka wandon nan dan dama tana sanye da rigar wanka, tana tunanin yanda zata saka rigar cikin sa'a shima saiya zauna gaban farantin data zuba naman nan, da sauri ta saka rigar ta cire waccen ta d'auki hijab ta saka, juyowa yayi zai mata magana yaga ta saka hijab, kallon da yake mata ne ya fahimtar da ita me yake nufi, "Ki cire shi ko na ci uwaki." Tasan ko magana zaiyi abinda zai fad'a kenan, dan haka ta rufawa kanta asiri ta cire ta aje ta zauna, kamota yayi ya zaunar da ita kan k'afafun shi ya d'ebo naman ya saka mata a baki, tun tana jin kunya tana sunkuyar da kai har ta daina tana karb'a, tace ta k'oshi tayi magiya ya barta haka amma yace ta k'oshi sosai ko ta iya...(al'amarinka ya fara damuna), haka suka kammala suka sake tsabtace kansu kafin suka kwanta, duk da tayi nesa dashi saida ya mirgino ya rumgumeta ta baya ya d'ora hab'arshi a wuyanta ya zagaya hannayenshi ta bayanta, kamar wanda za'a rabashi da ita haka ya rik'eta sosai, Amna dake jiran taji abinda zai faru sai kawai ji tayi numfashinshi ya sauya alamar bacci ya d'auke shi, saida ta k'ara d'aukar wani lokacin kafin ta iya samu ita ma bacci ya d'auke ta. *Safiya*... *Alhamdulillah* *Masoyan k'warai ina godiya, 'yan k'asata ba zan manta da hallacinku gare ni ba.* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _36_ Gaba d'aya baya jin dad'i tunda ya tashi, tunda ya ganta kusa dashi yaji baya tare da wannan zumud'in na son ya kasance da ita, tunanin abinda ya faru jiya ya tsaya masa a rai, duk da shine farko a wurinshi daya tab'a aure, amma yanda ita ce taja hankalinshi sai yanzu ne yake b'ata masa rai, ta nuna masa ita yar bariki ce, tabbas ya samu gamsuwa da ita, amma tunanin irin mazan da tayi mu'amula dasu, har yanzu yana ganin fuskar yaron nan da suka tab'a had'uwa lokacin da yaje wurinta. Har ga Allah, yau d'in nan duk yaji ta fice masa a rai, yana ji kamar ba zai iya rayuwa da wannan tunanin ba, dan zuciyarshi ba zata d'auka ba, zai kuwa iya jurar wannan matsin? Sukuku ya k'arasa shirinsa suka kammala karin kumallo wanda aka aiko musu daga cikin gida, duk da ta lura da yanayinshi ya canza amma da zai fita sai tace "Junaid ina so zan shiga cikin gidanku na gaisa da mutane, ina so nasan kowa kuma kowa ya sanni mu fahimci juna." Kallonta yayi a gatse, *Junaid*? Sunanshi ta kira gatsau haka? D'auke idonshi yayi daga kallonta yace "Ba damuwa, kije." Ficewa yayi wanda hakan ya matuk'ar b'ata mata rai, kutumar uba, ita zai cewa kije kuma ya tafiyarshi, me yasa bai ce su tafi tare ba tunda yasan ba ko ina ta sani ba? Lallai ma yaron nan a cewar ta, mik'ewa tayi ta shiga d'aki ta sake gyara shirinta ta yafa mayafi ta fito, tabbas ta ga k'ofar da taji ana cewa har da k'ofa da zata sadaka da cikin gidan, dan haka bata tsaya komai ba ta bud'a ta shigo, k'arewa gidan kallo take tana tunkarar babban falo, tsari da kyawun gidan ya birgeta sosai, ta kuma saka a ranta dole sai tayi gatsau gatsau ta hakane kawai zata iya tsallake rashin mutumcin da zata iya fuskanta, dan in tayi laushi zasu samu abun gori a kanta, shiga tayi falon da sallama tana sake kallon falon, Hajia da lokacin ta gama karyawa tana zaune, tana ganinta ta saki wata shegiyar dariya tace "Sanin wa Junaid ya auro min ya kawo cikin gida yasa ba zanyi mamakin ganinki a yanzu ba kuma anan." Murmushi Maryama tayi ta k'araso ciki tace "Kamar yanda nima banyi tunanin ganin mamaki a fuskar kowa ba saboda ganina." Cike da k'asaita Hajia tace "Wannan na d'aya daga cikin dalilan da suka na gujewa Junaid aurenki, bana son rashin kunya da fitsara a rayuwata." Ba tare data daina murmushi ba tace "Gashi kuma hakan har ya zama d'ab'iata ta yanda ba zan iya dainawa cikin sauk'i ba." Saida ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya tace "Ina fatan dai ya fad'a miki akwai doka da oda a gidan nan, kuma nice nan mai bayar da wannan doka da odar, dan haka ki iya bakinki kisan me zaki dinga fad'a min, da ban so ba da yanzu haka baka cikin gidan nan, kina can bakin titi kina neman wanda zai kwantaki ya baki na abinci." Kalaman sun mata zafi sosai, kuma wannan ne dama take gudu a auren Junaid, amma sai bata nuna ba tace "Bai fad'a min akwai mai bayar da doka da oda ba, watak'ila kuma bai fad'a min bane saboda yasan a inda ya d'auko ni, ina rayuwa ne cikin 'yanci babu mai hanani bare sakani, yana da tabbacin ba zanji maganar kowa ba anan shiyasa." Sake had'e fuska tayi tace "Ki fad'a min meya shigo dake nan kika baro b'angaren ku? Dan ban son kai da kawowa haka kawai." Murmushi ta mata sosai tace "Na zo gaishe da surukata ne." Da yatsa ta nuna mata d'akin Zeinabu tace "Ki wuce to ki gaggauta fitowa ki koma d'akin mijinki, dan ba zan lamunci rashin hankali ba." Zata wuce d'akin data nuna mata ta ji tace "Su sauran amaren ko suna ina?" Juyowa Maryama tayi zatayi magana sai kuma Hajia tace "Kai na manta fa, ashe su d'in tarbiyata ce, ba zasu tab'a yin wannan fitsarar ba." D'aga gira tayi tace "Har mu gani dai." Zata sake wucewa Hajia tace "Gashi kuwa muna gani a halin yanzu, da budurwa ya aura da watak'ila yanzu sai an taimaka miki, amma kash, da yake baiji magana ta ba gashi da k'afafunki kika shigo nan cike da k'aryar rashin kunya." Fitowar Ummy tare da Zeituna daga madafa sun gama gyara komai yasa Maryama yin shiru, ganin kamala a fuskar Ummy kuma dama tasan ita ce uwarsu Ammar saita gaisheta da ladabi, da fara'a Ummy ta amsa da "Lafiya lau amarya, ya kwanan bak'unta kuma?" Hajia ce ta katse da cewa "Kinga alamar bak'unta a tare da ita ne? Matar data shigo da kanta nan ba tare da ko rakiyar mijin ba, mtssss." Sunkuyar da kai sukayi hakan yasa Maryama kallonsu a ranta tace "Eh lallai, da alama wannan ita ce hawan jinin gidan nan, to wallahi idan ba tayi wasa ba ni zan k'asara ta kowa ma ya huta, ni ba zan d'auki wannan iskancin ba." Juyawa kawai tayi ta nufi d'akin Zeinabu, zata k'wank'wasa k'ofar wacce ke bud'e sai labulen d'akin da akayi ruf dashi sai kuma ta tsaya, kasa kunne tayi sosai jin muryar Inna na fad'in "Ya kamata dai ku sani duk son ku na kuga kun rufe sirrin nan wallahi ba zai rufu ba, dole wata rana gaskiya tayi halinta, munyi kuskure baya bai kamata mu ci gaba da zama cikin wannan kuskuren ba, babban laifi muka aikata da muka bari aka d'aura miki aure da ciki a jikinki, idan har baku fito kun fad'a ba kowa yasan halin da ake ciki, to fa ku sani matsalar zata farane daga lokacin da ta Allah ta kasance da colonel Hussein." Cike da damuwa Zeinabu tace "Inna nima sai yanzu na fara fahimtar hakan, na sani da ace a waccen lokacin muna da ilimi na addini da bamu yarda munyi aure da ciki ba, yanzu gashi shekaru sunja babu wanda yasan da al'amarin nan, ina jin kunya da tausayin Junaid idan yaji cewa an haifeshi kafin aure ne, hakan na nufin baya da gadon mahaifinshi, sannan waccen jarababbar matar bansan me zata iya yi ba idan ta sani." Inna ce tace "To sai me? Hajia tunda bata da wutar da zata saka ku duk hargaginta ai na banza ne, kuma karki damu da Junaid akan gadon ubanshi, tunda dai yana da aikinshi mai kyau da yake yi duk da ma bashi ya so ba, dan haka wannan ba damuwa bane." Shiru kawai Zeinabu tayi tana tunanin mafita, Inna ce tace "Kawai ki fad'awa colonel d'in dan kusan ta yanda zaku fad'awa wanda suka dace su sani, amma dai kuyi da hanzari dan rayuwa yanzu ba tabbas." Kallonta Zeinabu tayi tace "Kenan yanzu Inna kin yafe kud'in fa muke baki duk wata?" Dariya Inna tayi tace "Na yafe kam, amma ai dole kinsan dai nauyi na yana wuyanki." Dogon tsaki Zeinabu tayi a zuciyarta tace "Aikin banza, kamar ba ke kika bamu shawarar yin shiru ba a waccen lokacin." Maryama dake tsaye bakin k'ofa tana jin haka ta juya da k'arfi ta bar wajen, bata tsaya komai ba ta koma b'angaren ta, tana shiga d'aki ta cire mayafinta ta shiga safa da marwa a tsakiyar falon, lallai ita ma ta samu makamin yak'ar mutanen gidan nan, kenan mijin data aura kafin aure aka haifeshi? To ai gwara ma ni da banyi aure da ciki ba, da wannan tunanin ta kira Iklima tace ta kawo mata Huda tare da kayanta yarinya zata dawo gidan ubanta kawai, Iklima ta so ta bari har tayi sati d'aya amma tace ta kawota kawai, ba yanda ta iya ta shirya Huda wacce da za'a koma da ita Goure ta kawo mata ita. *Jumare* ce yau ta kawowa Zeituna ziyara, tunda suka shiga d'akin ta dama ta fad'a mata kawu Mamu ne ya turota yace ta zo ta karb'ar mishi kud'i zai siyi magani bashi da lafiya, hankalin Zeituna ya tashi jin ance bashi da lafiya, can bayan gidan b'angaren ajiyar bak'i taje ta samu lieutenant ta fad'a mishi, kud'i ya bata masu yawa yace ta bata kuma zasu zo duba shi anjima da dare, ko da ta kawo mata kud'in ta bata zata tafi saida ta tsaya gaban kayan shafe shafenta ta d'auki wanda take so kafin ta fito, tare suka fito ta rakota tana fad'a mata cewa "Jumare dan Allah ki rik'e kud'in nan da kyau karki jefar a hanya, dan na sanki da shiririta da son wasa." Daidai suna kawowa farfajiya daidai tana fad'in "Dallah ni ki rabu dani ko, me kika d'auke ni to da zan kasa rik'e wannan kud'in? Kawai gani kike kin haifeni saboda kin auri mai kud'i kin ci kin sha kinyi taib'a." Zeituna bata ji dad'in abinda ta fad'a ba, musamman da farfajiyar akwai mutane cikin bak'in da suke shirye shiryen komawa garuruwansu. Duk abinda ta fad'a kan kunnuwan *Ammar*, jar bala'i, wannan wace yarinya ce? Uban waye ubanta a duk area nan? Har cikin gidanta kuma take fad'a mata haka? Tana cikin tafiya ya taho cikin takon isa yana fad'in "'Yan mata ji mana." Cak Jumare ta tsaya tana kallonshi har ya zo kusanta, Zeituna da tasan yau yar uwarta ta had'u da daidai ita matsowa tayi ita ma tana kallonsu, saida ya kalleta sama da k'asa ya rik'e hab'a yace "Ke bafulatana ce?" Fuskar mutumin dake tattare da haiba da kwarjini ta bala'in firgitata, da k'yar ta iya cewa "Eh." Ta fad'a a hankali, jinjina kai yayi yace "Kina jin hausa sosai?" Zeituna ce tace "Tana ji ita ma." Ba tare daya kalli Zeituna ba yace "Kina iya gane kowane yare?" Jumare ce ta d'aga kai alamar eh, dan haka ya gyara tsayuwa yace "Alhamdulillah." Nuna Zeituna yayi yace "Wannan ya kike da ita?" Kallon Zeituna tayi tace "Adda Zeitu? aunty na ce." Cikin kafeta da ido yace "Kina nufin dai ita ke gaba da ke?" Da sauri ta kalleshi tace "Eh." *Gauuuu* ya d'auketa da wani bahagon mari, k'ara ta saki tare da sakin kayan hannunta ta durk'ushe, da sauri Zeituna ma ta durk'usa ta dafata, d'ago kai tayi ta kalleshi da nufin fad'a mishi wannan fa ita ba komai bane a wurinta, amma sai taji ya d'ora da "In kika bari na sake ganin wannan guntulallar k'afar taki a gidan nan wallahi sai kin gane kurenki, na kuma mareki kije ki turo ubanki kowaye shi, a shirye nake dana tsaya da kowa a gaban alk'ali indai akan uwata ne." Saida ya zuba hannun dama a aljihu ya fara takawa ya nufi falon Hajia, kamar an kirashi sai kuma ya tsaya ya sake dawowa ya sunkuya kusan fuskokinsu yace "Ke kalleni nan." D'agowa Jumare tayi ta kalleshi da jajayen idonta, saida ya mata alama yace "Kin fara hak'oran hankali ne?" Duk da tana jin hausa amma yanzu saiya gindayar da ita, kallon Zeituna tayi da alamar tambayar me yake nufi? A harshen fulatanci Zeituna ta mata magana, hakan yasa ta kalleshi cikin muryar kuka tace "Eh sun fito min." Murmushi ya mata yace "To nan gaba idan kika sake mata rashin kunya Allah su zan zubar miki, kin gane." Tsaye yayi yana kallonta yace "Ya sunanki?" Cikin kumburo baki da tsantsar fulatanci a bakinta tace "Jumare." Yatsina fuska yayi yace "Jumare kuma? Juma'a aka haife ki? To me yasa ba'a saka miki Jumma ba?" D'an zaro ido tayi ta kalleshi, Jumma? Uwa ta fa kenan? A tunaninta yasan sunan mahaifiyarta ne shiyasa ya mata wannan shagub'en, ganin kallon da take masa yasa shi kallon Zeituna yace "Uwa ya gajiyarku?" Bai kuma jira me za tace ba ya sa kai falon Hajia d'aukar magana, Zeituna kuma lallab'a Jumare tayi ta tafi gida, saida ta tafi ne tayi murmushi tana fatan hakan da yayi ya zama silar daidaita tsakaninta da Jumare. Inda Maryama ta bar Hajia nan ya sameta shima, sai dai akwai mutane a falon wanda wasu ke shirin tafiya wasu kuma sai anjima, daga ciki akwai dangin Ummy, gaba d'aya yayi jam'i yace "Ina gajiyarku?" Duka d'akin da lafiya lau suka amsa tare da d'orawa da "Ya taku gajiyar?" K'ala babu wanda yace ma sai zaunawa da yayi kusa da Hajia yana kallonta tana kallonshi ita ma, ganin kallon da suke ma juna yasa Hajia k'ara had'e fuska tace "Da wane rashin mutumcin ka shigo kuma yau? Dan wannan murmushin na ka ya bayyana shegantaka ta kawoka." Hannunta ya kamo ya sumbata sannan ya kalli idonta yace "Hajia ina godiya, Allah ya saka miki da alkairinsa, Allah ya zundumaki aljanna bayan kinsha ruwan khausara, Allah ya dawwamar da farin ciki a rayuwarki kamar yanda kika saka rayuwata farin ciki." Cike da shewa 'yan cikin d'akin suka saka tare da amsa mishi da "Ameen." Bai kulasu ba sai d'orawa da yayi da" Hajia ni kam babu abinda zan saka miki da shi a gidan duniyar nan, amma duk da haka zan sakawa 'yata ta farko sunanki." Kallonshi kawai take bata tanka masa ba, matsowa yayi sosai kusa da ita cikin tattausa murya yanda babu mai jinsu yace "Hajia maganar al'adar nan ce na zo k'arasawa, ance a rana irin ta yau namiji yana bayar da rak'umi ne ko kuma wata kyauta mai tsoka, to gaskiya ni na zauna nayi tunani na kasa tunano abinda zaiyi daidai da dank'waleliyar jikar nan taki, shiyasa nace bara na kawo kaina saiki fad'i abinda kike so nayi." Dai lokacin tayi murmushin zaka raina kanka tace "Komai idan na fad'a za kayi?" Cike da tabbatarwa yace "A shirye nake Hajiata." Ita ma saida ta sassauta murya tace "Jan rak'umi zaka kawo lafiyayye, saika had'o da kud'i million d'aya, sannan ka siya mata sark'a da d'an kunnai na zinariya, idan kayi haka ma ya wadatar." Tana fad'a ta d'an kawar da kanta alamar zaka gane kurenka, shi kuma murmushi ya mata yana shafa sumar kanshi, kafin yayi magana Allah ya kawo lieutenant d'akin, mik'ewa yayi da sauri ya tarbeshi yana fad'in "Yawwa Abba barka, kud'i nake so ka bani." 😂😂😂 Saida ya harareshi kafin ya mayar da hankalinshi kan mutanen d'akin suka gaisa sosai, daf da Hajia ya zo ya duk'a ya gaisheta, yana mik'ewa ya juya ashe Ammar na daf dashi a baya sai kuwa suka had'e, tsabar k'arfi yasa lieutenant yin baya yana neman fad'uwa, da azama Ammar ya tallaboshi baya, kallon jua sukayi ya sakar masa murmushi, d'aga shi yayi lieutenant kuma cikin fad'a yace "Meye haka wai? Yanzu dana fad'i kaji dad'i kenan?" "Amma ai baka fad'i ba, Abba ina tare da kai fa, haka ba zai faru ba sai in k'asa ce tarufe min idona." Cikin fad'a yace "To yanzu uban me kake so da kake biyata a baya kamar wutsiya?" Saida yasa hannaye aljihu kamar wani k'aramin yaro yace "Kud'i zaka bani?" Da mamaki yace "Kud'i kuma? Gashi kuma ban iya tuna ranar daka bani ajiyar kud'i ba." Turo baki yayi irin shagwab'a yace "Abba ba fa ajiya na baka ba, kai ne kawai zaka bani kyauta." Hanya ya kata zai fita yace "To bana da." Bin bayanshi yayi yana fad'in "Ni dai ka bani kawai, idan ban tambayeka ba wa zan tambaya? Kai kad'ai ne fa ubana a garin nan, kuma duk hidimar nan da akayi sisinka ban nema ba." Juyowa yayi yace "Amma uban wa ya biya maka sadaki?" "To ai kai ka biya na kowa da kowa, kaga kenan ba zanyi lissafi da wannan ba." Har saida ya kai bakin mota zai shiga ya rik'e murfin mota yace "Allah saika bani, in kuma kace ba zaka bayar ba zan je wajen abokaina nace su bani bashi, kaga ku za ama dariya ace d'a kuma jika ga ahalin Gaga amma ya rasa million biyu." Ba tare daya ankara ba lieutenant ya kai mishi bugu a k'eya yana fad'in "Dan ubanka yi sauri kaje, daga nan saika biya gidan redio da telebijin duk ka fad'a musu ni Hassan na k'i baka million biyu." Juyawa yayi yace "Shikenan zaku gani kam." Kallonshi lieutenant yayi, irin tafiyar nan ce idan yayi hushi, hakan kuma zai iya sawa yayi komai, iska ya furzar ya d'aga murya yace "Me za kayi dasu?" Juyowa yayi yana dariya har ya k'araso kusanshi yace "... *Yan nigeria Allah ya saka muku da alkairi.* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` _Bismillahir rahamanir rahim_ _37_ Juyowa yayi har ya k'araso kusanshi yace "Alawa zan siyo?" Jin abinda ya fad'a yasa lieutenant yi mishi kallon baka da hankali ko me? tsaki yayi yace "Zan tsaya nan sauraren wannan shirmen naka ne?" Kallonshi yayi tace "To Abba gashi na fad'a maka." Da k'arfi yace "Uwarka! Alawar uban me zaka siya ta million biyu? Ammar ka kiyaye ni fa." Kwalar rigarshi ya kama yana wasa dashi sannan yace "Zan fara tarawa jikokinka alawa ne." Girgiza kai kawai yayi cike da damuwa ya fito da k'aramin makulli a aljihunshi ya mik'a mishi yace "Ka samu mahaifiyarka." Karb'a yayi ya juya ba tare da yace komai ba, yana shiga falon Hajia ta kalleshi tace "K'aryar banza kawai, kud'in ma da za kayi birgar dasu baka da saika karb'a wajen ubanka." Murmushi ya mata yace "Magana sahihiya, kinji fa kema ubana kika ce, to idan bai min ba wa zai wa? Nine fa sanyin idanuyarshi na farko." Kai ta d'aga mishi alamar kai tafi can tare da fad'in "Kai dallah can, shalele shine sanyin idaniyar kowa a gidan nan." Kallon can ta matse muku ke da shalelen ya mata ya nufi d'akin Ummy, tana shirin fitowa suka had'e a k'ofar d'akin, mik'a mata makullin yayi yace "Inji Abba ki bani million biyu." Fizgar makullin tayi ta koma d'akin inda ya bi bayanta, juyowa tayi tace "Fice min a d'aki ka jira ni k'ofa." D'aga kafad'a yayi ya juyo ya tsaya k'ofar d'akin, tana d'auko mishi ta same shi da waya a kunnenshi yana amsawa, abinda taji yace kawai shine "Zan turo a duba ta, ni ina cikin cin amarci ne ba zan fara fita ba gaskiya." Ta gefen ido ta harareshi ta mik'a mishi kud'in, karb'a yayi yana kashe wayar tare da makullin, kallonta yayi irin ba wasan nan yace "Akwai majiyaciya a asibiti dake buk'atar kulawar d'aya daga cikinmu, Ummy kije ki duba ta." "Saboda me?" Ta fad'a a hassale, kallonta yayi yace "Saboda ni jiya aka d'aura min aure, ina hutu." Ganin tayi shiru bata da abun fad'a yasa shi wucewa yana fad'in "Duk kwanakin da kikayi ma ba kya zuwa da izinin wa?" Da kallo ta bishi a ranta tana fad'in "Ya zanyi ma wannan yasan ina da cikin? Zai iya sakani gaba yana min dariya, a k'arshe ma yace na tsufa da haihuwa." Iska ta furzar tace "Allah gamu gareka." Yana daf da isa wajen Hajia Hamna ta shigo falon da alama daga waje take, riga da wando ne jikinta irin kayan nan na indiya, sai dai tsagar dake da rigar gefe da gefe har saman k'ugun ta, kallabin dake kalar wandon k'arami ne wanda ke saman rabin kanta, k'ura mata ido yayi yana kallo, har ta fice bata kula da tsiyarshi ba, juyawa yayi ya bita da kallo, shi kam ya fara gajiya da wannan yanayin da yake tsintar kanshi a ciki a duk sanda ya ganta, al'amarin girmama yake ba raguwa ba, har zuciyarshi canza salon bugawa take idan suka had'u. Hankalinshi yafi tafiya ga shigar data fita da ita, akan me Hamna bata jin magana? Me yasa ba zata taimaka mishi ba ta dinga rufe jikinta? Me yasa bata son kwanciyar hankalinshi ne? Hasalima bata damu da damuwarshi ba? *Ba zan lamunta ba gaskiya*, yana fad'in haka ya daka mata tsawa yace "Ke." Hamna data fara taka makala ko juyowa ba tayi ba, da k'arfi ya sake cewa "Kankana ke." Hajia dake zaune tana kallonshi ne tace "Wai kai ba zaka daina kiranta kankanar nan ba?" Kallonta yayi fuskarshi a had'e rai b'ace yace "Akan me zan daina? A baya ma na kirata haka bare yanzu dana tabbatar." "Ka tabbatar dame?" Ta fad'a tana kallon idonshi, Ummy dake tsaye k'ofar d'aki tana nata jimamin tana jin haka ta zaburo tana dariya tace "Ya riga daya saba ne Hajia, zai daina ai." Kallon Ummy yayi wacce baiga komai ba a idonta sai tsoro, wato ta d'auka zai fad'a ne? Shi data barshi ma ya fad'a mata yanda zata fahimta, kai shi fa yanzu zai iya fad'a in ya so ayi duk wacce za ayi, sai lokacin ya kalli Hamna data juyo tana hararenshi, yana ganin haka ya bi ta bayan kujerar Hajia ya taka wurinta, da yatsa yake nuna kanshi yana fad'in "Ni dai kika harara ko? Bari kiga iskanci." Ai da gudu ta fara haurawa sama dan tasan tsaf zai mata iskancin kamar yanda ya fad'a, tana kaiwa ta mayar da k'ofar ta rufe, Ummy dake binshi da kallo kar ya ja mata magana yasa take fad'in "Dawo, kar tab'a min yarinya wallahi." Tab'e baki Hajia tayi dan ita dramarsu bata dameta ba dama, yana zuwa k'afa yasa ya tura k'ofar sai kawai ta bud'e, baya tayi da sauri tana nuna shi tana fad'in "Allah ka fita a d'akin nan, Ummy, Abba zai kashe ni." Murmushin gefen labb'a yayi yace "Kinga kuwa banyi tunanin haka ba." Da mamakin me yake nufi ta kalle shi, fahimtar da ita yayi ta hanyar fad'in "Eh mana, sai yanzu ne kika fad'a min cewa kasheki ne kad'ai zai zama maganin matsalata." Da k'arfi ya shak'o wuyanta da hannu d'aya, fitowa yayi da ita a haka yana fad'in "Ban fad'a miki ki dinga saka hijabi ba? Ban fad'a miki ki daina saka wannan d'an banzan gashin ba? Raina ni ne kikayi kenan da ban isa na fad'a miki kiji ba." Ummy da su Zeinabu da Zeituna suna ganin ya fito da ita a haka suka rik'e baki, Ummy ce ta tunkare shi ta fara k'ok'arin b'anb'are hannunshi tana fad'in "Wallahi saketa, Ammar kar ka kashe min yarinya, bana son iskanci fa." Saida ya kawota gaban Hajia ya watsota daf da k'afafunta ta fad'i k'asa, rik'e wuyanta tayi tana wahalallen tari da hawaye tsabar wahala, Hajia ya kalla yace "Madame Suley, ki zama shaidata, Allah kar na karya yarinyar nan wani yace zai tambayeni dalili, ki fad'a mata kar ta sake fita babu hijabi jikinta, sannan wannan gashin." Ya fad'a yana kamo gashin da hannunshi yaja da k'arfi wanda yasa ta saki k'ara da k'arfi tana rik'e hannunshi, d'orawa yayi da "Idan na sake ganinta dashi reza zan saka na yake shi har da asalin gashinta." Sakinta yayi hakan yasa ta tashi da sauri tayi baya tana hararenshi, Hajia ce ta wurga mata harara tace "Sa'anki ne shi da kike hararenshi?" Sunkuyar da kai tayi tana k'ara jan d'an kwalinta saman kanta, a tsawace Hajia tace "B'ace min da gani malama." Rai a b'ace Hamna ta taka da sauri tana d'an bubbuga k'afafu tana gunguni kamar za tayi kuka, da kallo ya bita har ta haye sama sannan yayi k'wafa ya kalli Hajia, wannan kud'in ya mik'a mata yana murmushin shegantaka yace "Ga wannan ko, ni a wurina tafi k'arfin rak'umi d'aya sai biyu." Juyawa yayi zai fita ya kalli Ummy dake tunanin abinda ke tsakaninshi da Hajia, rak'umi biyu? Tab'e baki tayi irin Allah ya shiryakan nan kafin ta juya ta nufi d'akin ta, murmushin gefen labb'a yayi ya bar d'akin. Wannan al'amari ne da ba zata d'auka ba, a gidanta? A ahalinta har za'a samu wacce za tayi iko da 'ya'yanta? Wannan ba abu bane mai yiwuwa! Waya ta d'auka ta danna mishi kira, a daidai lokacin da uwar gida ta tsare gaba ta tsare baya. Ya sani a gidanshi Aissata ce ke mulkarshi, a gidansu kuma Hajia ke juyashi, a waje kuma shi yake nasa mulkin, tunda Aissata ta ga sunan wanda ya kira ta hana shi d'aukar wayar cike da kwarkwasa, sai dai hankalinsa na wajen bala'in da zai jawa kanshi, saida ya gama da duk buk'atunta kad'ai ta barshi ya fito daga d'akin da aka saukesu, mugun fad'uwa gabansa keyi da tunanin abinda zai tarar, hatta salon tafiyarsa saida ya canza zuwa kamar wanda aka cirewa lakka, da sallama ya shigo falon murya k'asa k'asa yana d'an tattare jalabiyarsa har bak'in wandonsa na fitowa, yana hango fuskarta kwarjininta yasa shi yin k'asa da kanshi, har saida ya ji kamar zaiyi fitsari tsabar razana, dan yasa ba zata duba mutanen dake kai da kawo ba suna shirin barin garin ba tsaf zata wankesa wankin babban bargo, duk wanda suka gaishe shi kasa amsawa yayi sai yak'e daya musu dan kar suce bai amsa ba, yana zuwa gabanta ya durk'usa da fad'in "In..." Bata bari ya gama fad'a ba ta mik'e tsaye tace "Bana son gaisuwarka, Haruna ku tattara naku ya-naku ku bar min gida tunda an gama abinda ya kawoku, idan ba haka ba wallahi zan tsinkawa matarka rashin mutuncin da kare ma ba zai ci ba." Hanya ta kama da sauri ta nufi kusurwar da zata sadata da d'akin ta, shafa gashin kanshi yayi yace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un." Mik'ewa yayi jiki a sanyaye ya bita d'akin, yayi sa'ar bata rufe ba dan haka ya shiga ya sake durk'usawa ba tare da sun had'a ido ba, cikin sigar rarrashi yace "Hajia dan Allah kiyi hak'uri ki gafarce mu, duk da dai bansan laifin da mukayi ba, amma Aissata bata..." "Bata da me? Me kake so kace?" Ta fad'a wa k'arfi, nuna kanta tayi tana fad'in "Har ni zaka nuna banda mahimmanci a gurinka, sanin kanka ne Gambo na juya jikokina ma bare ku dana haifa, har ka kwana cikin gidan nan ka bari rana ta fito ba tare da ka zo inda nake ba, wai sai yanzu ne k'arfe *01:00* rana zaka shigo min falo, kuma a hakan ma bayan na kira ka baka d'auka ba, shine har zaka ce baka san laifin daka min ba, to yayi kyau nagode, ka tashi ka bar min d'aki." Marairaice yayi yace "Dan Allah Hajia kiyi hak'uri, gajiya ce tasa dukanmu mukayi bacci mai nauyi, kiranki ma ban gani ba sai yanzu ina farkawa, kiyi hak'uri dan Allah ki yafe min, insha Allahu zuwa gobe zamu koma dama." Da yatsa ta nuna shi tace "Wallahi ba zaku sake kwana anan ba, ku had'a kayanku ku koma kaji na fad'a maka, in ba haka ranka zai b'ace fiye da tunaninka, kaje can ka k'arata tunda ka zama lusari shashashan da mace ke juyawa." Sululu ya mik'e yana fad'in "Allah ya huci zuciyarki Hajia, kiyi hak'uri dan Allah zamu tafi." Da kallo ta bishi tana tunanin idan tayi haka ai ba tayi nasara akan Aissata ba, kenan zata hak'ura da d'anta ne ta bar ma wata cen? Ai tak'amarta yana nesa dasu daga ita sai danginta ke morarshi, dan haka za tayi abinda zata k'untata mata ta nuna ita ma ta isa da shi, murmushin mugunta tayi ta zauna bakin gado tana jiran su tashi tafiya. Cikin tsananin damuwa Jibril yace "Abba ku fad'a min abinda ke faruwa mana, tun jiya gaba d'ayanku kun canza, Hajia har kuka na ga tana yi, kai ma kuma Abba ka shiga damuwa waccen ta kasa b'oyuwa, sannan Alhaji ma na fahimci haka daga gare shi, gaba d'aya kun sani rud'ani, dan Allah ka fad'a min abinda ke damunku." Shiru yayi, tunani yake ya fad'a mishi ko kuma yayi shiru, to idan ma yayi shiru wata rana fa shima zai zo ya sani kamar yanda shima ya sani bayan wannan shekarun, sannan yana da hakk'in ya sani shima dan ya shafe shi. Ajiyar zuciya ya sauke ya kalleshi cikin nutsuwa yace "Jibril, daga ni har kai mun kasance muna son sani iyalenmu na d'aya b'angaren, ni da kai duka mun yarda da k'addarar da ubangiji ya d'ora mana, wannan iyalen namu da muke son sani ne muka san su jiya, shiyasa kaga duk kowa ya shiga damuwa, domin kuwa wanda ya na gani a matsayin mahaifia sam babu wanda yayi tsammanin haka." Me Jibril zaiyi inba dariya ba yaji labarin kakanshi, da tsantsar fara'a yace "Abba da gaske? Wai kakana yana raye? Alhamdulillah, Abba waye shi? Fad'a min naji dan Allah na k'agu." Kallonshi yayi babu kuzari a tare da shi yace "Kasan wannan tsohon malam Rabi'u? Kakan Maryama matar Junaid? To shine." Saida yaji kanshi ya sara, malam Rabi'u kuma? Maryama kenan yar uwarsa ce ta jini? Kaga wani ikon Allah, kallon mahaifinshi yayi yace "Abba Maryama yar uwarta ce?" Cikin tab'e baki yace "Hakan alamu nuna." Dariya Junaid yayi yace "Abba alamu kuma? Ai abune a zahiri, Abba kawai kayi farin ciki kaima." Kallon Junaid yayi da mamaki, sai dai bai ce mishi komai ba, Junaid kam murmushi yake inda yake son wata rana Maryama ta nemi gaya mishi maganar banza, saiya zauna ya bud'e mata littafin rashin mutumci, dan saiya yagata ya nuna mata ba'a kanshi aka fara ba. *BADAK'ALA* *BADAK'ALA* *BADAK'ALOLI* Ko da Ammar ya koma kai tsaye madafa ya nufa inda yake jin motsin mutum, da shigarshi ya tunkareta cikin fad'a yana fizge karotte da wuk'ar hannunta yana fad'in "Dallah bani nan malama, ubanwa yace ki shigo nan? Daga zuwanmu jiya sai wani d'ora girki, to kiji da kyau daga yanzu har kwana shida ba zakiyi girki ba." Za tayi magana sai ji tayi ya kimkimeta ya fito da ita ya nufi d'aki, wutsil wutsil ta fara da k'afafu ta rufe ido gam ta sunne kanta a k'irjin shi, kallonta yayi yace "Ina fatan dai a k'oshe kike?" Shiru tayi, ba zata iya magana ba dan numfashinta ma taji ya sauya mata, bai sake magana saida suka shiga ciki ya sauketa kan gado ya kalleta, saida ya had'e alamar ba wasa ya nuna ta yace "Karki gusa daga inda kike." Girgiza kai tayi cike da tsoronshi a idonta, dan daga jiya zuwa yau ya gundureta matuk'ar gundura, yana da shan kai da takurar tsiya, safiyar yau ma wanka ya dage saiya mata saida tayi kuka ta rok'eshi ya k'yale ta, yanzu kuma bata san me yake nufi da kawota kan gadon ba da rana tsaka haka. Tana kallo ya fita daga d'akin, ba jimawa ya shigo da faranti a hannunshi, yana zuwa ya aje farantin ya juya yasa makulli a k'ofa ya dawo, matsakaitan idonta ta zuba mishi tana had'e yawu masu d'aci d'aci, hannunta ya kamo ya shiga ban d'aki da ita, zip d'in rigarta ya zuge yana neman zage rigar daga jikinta, da sauri tasa hannayenta a k'irjinta tana kallonshi tana shirin fashewa da kuka, kallonta yayi ranshi a b'ace ya saketa, juyawa yayi ya d'auko soson wankanta, yana juyowa ya had'e hannayenta biyu, had'a ta yayi da bango ya matseta ya d'aure mata hannayenta ta baya, kafeta yayi da ido yana zare rigar daga jikinta, girgiza kai ta shiga yi kamar zata cire shi, lab'e baki tayi irin yaro zaiyi kuka hakan yasa shi cewa "Inban zubar miki da hak'ora ba Amna ki ce d'an iska ne ni, wallahi kiyi hankali dani kar kiga ina d'aga miki k'afa, dan kina amarya ne shiyasa." Duk yanda ta so rufe jikinta kasawa tayi saida ya mata zigidir kamar yanda ta fad'o duniya, ba zato ba tsammani taji bakinshi a kan kan... *Ma'assalm* *Alhamdulillah* 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ (sai Allah) *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura...)_ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 *AHALI NA*👨‍👩‍👧‍👦 ©🌠 *🇳🇪TAURARIN NIGER..* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` ✪{T . N}✪📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurarin-Niger-100155928500614/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _38_ Da k'yar ya rabu da ita ya d'ago kai ya kalleta, hawaye sharkaf a fuskarta, kuka taka sosai kamar dukan tsiya ya mata, wurga idonshi yayi irin ya damu d'in nan tare da ja baya, juyowa yayi ya fito daga ban d'akin yana fad'in "Zo nan." Bata kula shi ba saida ya fita, rigarta ta mayar sannan ta wanke fuskarta ta fito, k'ura mata ido yayi harta zo ta zauna kusa da inda ya nuna mata, k'asa tayi da kanta bata da niyyar kallonshi, dan haka ya jawo farantin nan gabanshi ya d'auki wuk'a ya fara yanka lemun yana sha yana kallonta, lokaci lokaci yakan saci kallonta amma ta k'i d'agowa, aje lemun hannunshi yayi ya kamo nata hannun ya taso wa ida, zaunar da ita yayi akan cinyar shi hakan yasa ta rintse ido sosai, wuk'ar nan ya d'ora mata a wuya yace "Kalle ni." Tana bud'a ido taga wuk'a ce ya aza mata bata san lokacin data kwamtsa k'ara ba tasa hannayenta ta rufe fuska, lumshe ido yayi sanda siririyar muryarta ta daki kunnuwanshi, gaba d'aya jikinshi saida ya amsa, bud'e ido yayi ya aje wuk'ar ya d'auki lemu, janye hannayenta yayi yasa mata lemun a baki, amsa tayi tana sake sunne kanta, cikin taushin murya yace "Amna, kafin a d'aura aurenmu na d'auka ni dake zamu zama kamar abokan juna ne, amma gashi daga jiya zuwa yau naga sai k'ara tsorata dani kike, ba haka nake so mu zama ba Amna, ina so naga kin zama komai tawa wacce zan iya samun farin ciki a wurinki, ina so ki zama sirrin farin cikina, zan so ki zama maganin damuwata, Amna burina shine ki zama mai share hawaye na a duk sanda suka kwaranyo, Amna ki zama aminiyata kuma abokiyar shawarata, Amna *banda kowa*, sannan *banda komai*, babu wanda yake *kusanta ta*, ina so ki zama tare dani a kowane hali kuma a kowane yanayi, na sani Amna gidan nan ko kuma nace duk ahalinmu suna min kallon wani mahaukaci kuma marar kunya fitsararre marar tarbiyya, amma...amma..." Sunkuyar da kai yayi yana furzar da wata zazzafar iska daga bakinshi, rawa muryarshi keyi kamar zaiyi kuka, zuciyarshi bugawa ta fara yi da sauri sauri, ya jima kanshi na kallon k'asa kafin ya d'ago yana kallonta sai dai basu had'a ido ba, bud'a baki yayi a hankali yace "Amna ni ba mahaukaci bane, ni ba marar tarbiyya bane, sannan ina da kunya da nutsuwa, duk abinda nake yi ina sane nake yin shi, da gangan nake yi da fatan samun kusanci a wurin iyayena, amma..." Da sauri yasa bayan hannunshi ya goge yar k'wallar data taho mishi, da sauri ya turata gefenshi ta fad'a kan gado shi kuma ya mik'e tsaye, juya mata baya yayi yace "Har yanzu ban yi nasara, na d'auka zasu iya zama dani suji dalilin da yasa na zama haka, sun kasa fahimta har yanzu, babu mai iya gane ina jin yunwa ko na k'oshi, to tayaya ne zasu iya fahimtar abinda ke zuciyata, na zab'i na fara fito dashi ne dan kar ciwon zuciya ya kama ni a k'arshe na mutu, bansan ya zanyi da su ba." Juyowa yayi ya kalleta wacce ita ma ta k'ura mishi ido yace "Na gaza Amna." Ban d'aki ya shige ya barta zaune, k'urawa k'ofar ido tayi tana tunani da nanata abinda ya fad'a, ta d'an jima a haka kafin ta d'aga kafad'u tare da tab'e baki ta mik'e ta koma madafa, girkin data jima da d'orawa ta ci gaba daga inda ta tsaya, sai dai jikinta a matuk'ar sanyaye yake tana tunanin halin da mijinta ke ciki, meye damuwarsa? Meye tsakaninshi dasu Ummy? Meye ainihin abinda ke faruwa? Hak'ik'a ko ita kafin yanzu tana jin yana matsa mata ne sosai, tana ji babu kunya a al'amuransa, yana da k'arancin nutsuwa wani lokacin, kenan duk yana sane yake yi? To me yasa? Me yasa namiji kamar Ammar ke saurin zubar da hawaye? Bayan ita shaida ce akan jarumtarsa wacce ke tattare da masifa da bala'i, a sanin data mishi ko baka nemi jaraba da shi ba shi zai nemeka da ita, a sanin data mishi baya da saurin kasawa haka, mutumin ne dake tsaye tsayin daka wajen ganin ya ci galaba akan abokin karawarshi, to amma meya raunata zuciyarshi har haka? Wannan amsa ce daya kamata tasan amsarta, domin yanzu alhakin farin cikinshi na wuyanta ne, da haka ta k'arasa girkinta ta fito ta gyara wurin cin abincin, ta nufi hanyar da zata sadata da d'akinta taga ya fito daga d'aya d'akin cikin k'ananan kaya, amma abun mamaki bai yarda ya had'a ido da ita ba. Ya nufi hanyar fita tayi saurin cewa "Yah Ammar." Tsayawa yayi ya juyo ya kalleta amma baice komai ba, shagwab'ar da fuskarta tayi kamar ta jarirai tace "Abincinka fa." Har ga Allah da ya so irin d'aurawer nan, amma yanayin da tayi da fuskarta saiya sashi sakin murmushi, domin kuwa abinda ya zo masa a rai ita ce Hamna, wato Hamna tafi k'warewa wajen shagwab'ar bubbuga k'afafu, ita kuma wannan gaba d'aya take canza fuskarta da yanayinta idan zatayi ta ta shagwab'ar, d'aga gira yayi yace "Kenan saida kika dafa abincin?" Nufowa kanta yayi yana k'ok'arin cire belt d'in shi yana fad'in "Idan na rugurguza miki jiki gobe ba zaki sake bijirewa abinda na fad'a ba." Tana ganin ta durk'ushe ta had'e hannaye biyu tasa kusa tana fad'in "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri ba zan k'ara ba wallahi, idan kana so ma yanzu sai nake na zubar da wanda na dafa, dan Allah karka dake ni wallahi bana son duka a jiki na." Ganin ya kawo daf da ita amma bai cire belt d'in ba yasa ta rintse ido, yana zuwa yasa hannayenshi ya tallabota yana dariya yana kallon fuskarta, ganin bata bud'a idon ba tsabar tsorata da tayi yasa shi rumgumeta jikinshi yana fad'in "Amna yanzu fa na gama fad'a miki, shin idan ban zolayeki wa zan zolaya?" Shiru tayi daga kukan da take rerawa ta bud'a ido ta d'ago kai ta kalleshi, yanda idonsu suka had'u ne yasa kowannensu jin wata wutar tsartsatsi ta bulbulo daga zuciyarsu, murmushi ya dalla mata ya tallabe fuskarta yace "Irin rayuwar da nake so muyi dake kenan Amna, mai cike da mutuntawa, farin ciki, annashuwa, k'aunar juna, tsokana da zolaya." Sunkuyar da kanta tayi a cikin k'irjinshi, shi ma kuma yana jin haka saiya k'ara kwantar da ita yana shafa kanta yana sauke mata numfashi a kai, sanyanyen turarenshi mai tayar da tsikar jiki da kuma kwantar da hankali take shak'ar k'amshinsa, luf tayi kamar mai son yin bacci tare da zura hannayenta ta baya ita ma ta d'an rik'e shi amma ba sosai ba, tunanin duniya take a daidai wannan lokacin. Ammar dai, yayansu dake matuk'ar firgita lissafinsu, wanda basa fatan a kai mishi k'ararsu idan sunyi laifi, wanda ko babu laifin ma zai iya kunyataka ya tsinka ka a cikin jama'a, yau ita ce a k'irjin shi a matsayin mata? Bata tab'a kawo haka a ranta ba, dan a wajenta abune da ba zai yiwu ba, tayi tunanin tsaf zai nuna ta yace baya sonta, ta d'auka zai kalleta ne yace Allahya tsare shi da aurenta. Kai ita kanta fa taso tace bata son shi, amma ganin shi bai furta ba yasa ta yin shiru da fammun d'inta, dan idan har ta kuskura kalmar bana sonka ta fito daga bakinta, to tsaf zai iya tisata a gaba da tab'arya yace sai yaji dalili, wannan dalilin ne ita kuma yasa bata iya fad'a ba. Tana wannan duniyar taji ya d'ago kanta ya kalleta yace "Kin iya girki ne dama?" Kallonshi tayi a sagale, na iya girki? Me yake nufi? Kafin ta bashi amsa ya nufi wajen abincin yana fad'in "Na ga dai waccen kakar taku tafi damuwa da al'amarin tsaronku ta yanda bata barinku fita, amma kulawa daku kuma wannan bata ma san me takeyi ba." Bin bayanshi tayi ya zauna kan kujera ita kuma ta fara zuba mishi farar shinkafar da tayi warwara gwanin kyau, sai kabeji data zagayeta da su sannan ta kuma zagayeta da karas wanda duk ta gurzasu, sai dunk'ulallen naman data jera shima kafin ta zuba sauce d'in albassar a tsakiya, tab'e baki yayi ya janyo farantin ya d'auki cokali ya kai lomar farko, kallonta yayi ya mata alama da hannu 👌cewa komai yayi, murmushi tayi ta ja kujera ta zauna cikin d'ard'ar tace "Ai ba ido kawai Hajia take saka mana ba, har yanda zamu kyautata rayuwarmu tasa an koya mana." Murmushin baki da hankali ya mata ba tare daya kalleta ba, saida yayi loma bakwai har ta manta da zaiyi magana sannan taji yace "Amna." "Um." Ta fad'a tana mayar da hankalinta kanshi, saida ya kalleta yayi kalar tausayi sosai yace "Dan Allah ki dinga girka min abinci kullum ina ci, ina yawon zama da yunwa, ki min wannan alfarmar kinji?" "To amma yah Ammar me yasa baka san cin abinci?" Kallonta yayi babu annuri a fuskarshi, har zai bata amsa sai kuma ya canza maganar yace "Bana da wanda zai rik'a bani a baki ne." Sunkuyar da kai tayi a zuciyarta tace "Uban wani kakan wani ka zauna sai an baka abinci a baki? Lallai ma mutumin nan." Kafin wata magana ta sake shiga tsakaninsu aka bud'a k'ofar d'akin aka shigo, dukansu kallon k'ofar sukayi a tare, da sakin fuska Amna tace "Autan Ummy ne?" Bai ce komai ba kamar yanda bai saki fuskarsa daga had'ewar daya mata ba, saida ya zo inda suke yace "Zuba min nima zan ci." Murmushi tayi tana kallonsa ta fara k'ok'arin zuba masa tana fad'in "Autan Ummy kamar ranka a b'ace? Waya tab'aka ne?" Kujera yaja zai zauna Ammar ya sauke mishi jajayen idonshi, kallo ne da zai iya saka fitsari a wando, kallo ne dake tattare da aika sak'onni dayawa, ba kayi sallama ba, baka gaishe da mutane ba, sannan kana wani d'aurawa mutane fuska, baka ga wurin zama ba sai a nan? Sannan me ma ya kawo ka?😂 To bashi Amsa Kamal. Kallon Amna yayi wacce ita ma ta kalleshi dan ta lura da kallon daya mishi, murmushi ta sake yi tace "Wai waya tab'a ka ne Kamal?" Turo baki yayi yace "Tonton Gambo ne zai koma Niamey yanzu, shine na ce zan bishi Hajia tace a'a, wai sai dai su tafi da Hamna." Dukansu sake bashi hankalinsu sukayi inda Ammar ya d'ora da cewa "Saboda me?" "Nima ban sani ba." Ya fad'a yana zaunawa kan kujerar, kallonshi Amna tayi da mamaki tace "Me yasa Hajia zata tura Hamna can kuma?" "Ba haka kawai tayi ba." Yana fad'a ya mik'e da hanzari zai bar falon, da sauri Amna ta bi bayanshi tace "Yah Ammar zan iya zuwa na ga yer uwata? Wallahi nasan ba'a son ranta zata je ba, daga ni har ita babu mai son zuwa wajen Abba saboda tanti Aissata ba k'aunarmu take ba." Hannunta ya kamo kawai suka fita, ta k'ofar dake cikin gidan suka shiga, kai tsaye falo suka nufa ba tare daya saki hannunta ba, suna shiga Amna tayi sallama amma banda gogan, hankalinshi na kan mutanen dake cikin d'akin yana kallonsu d'aya bayan d'aya, a hankali ya saki hannunta ta gaishe da mutanen wurin, kowa ya amsa amma banda Hajia dake kallonta a hargitse, kallon mahaifinsu tayi dake zaune kan. kujera tace "Abba yanzu zaku tafi?" "Yanzu zamu koma auta ta, amma tare da Hamna zan tafi." Duk yayi maganar ne jiki a sanyaye, da d'an mamaki tace "Amma Abba me yasa zaka tafi da ita yanzu? Kai fa kake cewa kafi son zamanmu anan." "Yanzu kuma ya sauya, zai tafi da ita tunda anyi hutu, kuma ba aure ne da ita ba tunda ta k'i aure." A tare suka kalleta ita da Ammar, kallon ladabi da tsoro ta mata, yayin da shi kuma ya bita da kallon to sai akayi yaya kuma? Hajia kifa kiyaye ni, meye na wani d'auketa daga nan d'in? Jin bbu wanda yace wani abu yasa Amna ta tunkari d'akinsu na sama da sauri dan ta samu Hamna, tana shiga ta sameta zaune bakin gado da alama kuka take, k'arasawa tayi ta zauna kusanta ta dafata tace "Rabin jikina, kuka kike? Na sani dama ba zaki so tafiya ba, amma me yasa Hajia tace a tafi dake?" D'an d'ago kanta tayi ta kalleta tace "Nima bansan dalilinta ba rabin jiki, kawai dan bata son gani na a gidan nan." Da sauri tace "A'a rabin jiki, karki fad'i haka mana, kinfi kowa sanin yanda Hajia bata san muyi nesa da ita, ina ga dai ko dan baki amince da auren yah Junaid bane." Tab'e baki tayi alamar ko oho, jin ba tace komai ba yasa Amna mik'ewa tsaye ta kamata tana fad'in"Taso, tashi muje ki bata hak'uri dan Allah, ba zan yarda ta rabani dake ba a lokacin da nafi buk'atarki a kusa da ni." Mik'ewa tayi cike da kasala tace "Amna ba zata hak'ura ba, kefa kin sani." Janta tayi da k'arfi suka nufi hanyar fita, a lokacin ne wani tunani ya zo ma Hamna, a take sai taji tana buk'atar yin nisa da gidan ma ko dan yer uwarta, dan har yanzu bata iya kallon k'wayar idonta idan ta tuna tasan mijinta kafin ita, duk da tursasata akayi amma abun kunya ne a wurinta. Sai dai kuma Ummy na buk'atar zamanta anan ko dan abinda ke cikinta, *ciki?* Shine abinda ta sake maimaitawa, hawaye taji sun taho mata a wannan lokacin, bata ankara ba sai ji tayi sua sauka kan matattakala suna sauka k'asa, yanayinta ne ya sake canzawa gaba d'aya, sanyin jijiyoyinta suka rub'anya ta yanda suke daf da tsinkewa, tun daga nesa take kallon mutanen dake k'asa, hawayen ne ke ci gaba da zubo mata saboda tasan a halin yanzu yer uwarta ba zata ji dad'in abinda zata mata ba, dan kuwa k'aryata ta ne zatayi a gaban mutane, tasan za taji zafi sosai sai dai zata fahimci dalilinta, sai dai kuma bata san yaushe ne ba?. Tunda suka taho ya k'ura mata ido, kallon k'wak'waf ne yake mata na son gano yanayin da take ciki, sai dai garin kallon nan na jaraba ne ya fara hango wani abun, canji ne sosai wanda shi dai bai santa da shi ba, amma ganin baida hujjar da zai tabbatarwa kanshi yasa shi faa fafutukar neman hujjar, bai daina binta da wannan kallon mai firgita wanda ake ma ba suka k'araso, Amna na rik'e da hannunta suka tunkari wurin Hajia da niyyar mata magana, amma sai Ammar yasha gabansu kamar sojon da zai bincikesu, idon Hamna ya kalla sosai tare da mata wani tuhumammen kallo ya nuna idonta da yatsa kamar zai tsoneta yace "Sai kace wata mai ciki sai k'yak'yabta ido kike, ko tafiyarce ba kya so?" Wandon dake jikin Ummy ne kawai ya mata shamaki da saurin b'allowar fitsari, sai dai ta tabbatar kayan cikinta zamansu ya sauya, dan juyawar da sukayi mota ce kawai za tayi wannan harurun da kai yayin da ta jirkice ta fantsama katantawwa da kai. Hamna kuma numfashinta ne taji ta nema ta rasa, hakan ne ya haddasa mata rufe ido sai k'wayar idonta dake juyawa, Amna kuma kallonshi tayi ba tare da tunanin komai ba tana murmushi, dan ita yanzu ta fara fahimtar mijin nata, sannan da yace yana sane yake komai yasa tayi damarar shanye duk wata katob'ara tashi, kowa madale wajen abinda yayi tunani kenan ba Hajia kad'ai ba, wato rashin kunyar ce ko? Kamar a mafarki sai gani sukayi yasa hannu ya tallaba kanta yana k'ok'arin bud'e mata ido, dan shi dai a matsayinshi na likita duk da ba abinda ya karanta ba kenan, amma da kallo da kuma ji zai iya gane larurar wani majinyacin, yana cikin kiciniyar nan Ummy dake kallonsa kamar mahaukaci ganin yana neman b'alle mata lik'i yasa ta tahowa da k'arfin tsiya, k'arfin da yafi k'arfin kuzarinta da d'ab'iarta, tana zuwa gabanshi ta d'aga hannu iya k'arfinta ta wanke fuskarshi da mari. K'arfin marin yasa shi duk'ar da kai gefe d'aya dafe da kunci, ya jima haka yana sauraron masifar da Ummy ke mishi, cikin hargagi da zautuwar tunani take fad'in "Baka da hankali ne? Wannan wace irin fitsara ce? A gidan uban wa ka koyo wannan tarbiyar? Anya Ammar kai d'ana ne kuwa? Ka sani fa a hanyar aure na same ka ba da zina ba." Hannun Hamna ta kama da niyyar barin wurin taji Hajia tace "... *Saboda farin cikin isar da yarinyata lafiya d'akin mijinta.*💃 09/09/2020 à 17:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ (sai Allah) *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura...)_ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 *AHALI NA*👨‍👩‍👧‍👦 ©🌠 *🇳🇪TAURARIN NIGER..* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` ✪{T . N}✪📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurarin-Niger-100155928500614/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _39_ Hajia ce tace "Malama meye na tunzura haka? So kike ki rufe bakinmu mu kasa fad'ar rashin kunyar d'an ki? To dawo da ita tafiya zasuyi." Juyowa sukayi suka tsaya sai rarraba ido suke alamar rashin gaskiya, a lokacin ne Hajia ta kalli Hamna da kyau, kallabi ne jikinta wanda bai rufe mata jiki ba, tabbas Hajia tasan ita da Amna ba ma'abota bras bane, dan gabansu a cike yake kuma pampam dashi, su Umaimah ne sarakan sawa kullum, amma ganin yau sun mata wata irin cikowa kamar mai ciki yasa ita kanta sai taji ba dan Ammar ba mutuminta bane data yarda da abinda ya fad'a, Ummy dake cike da razani da tsoro tuni ta ga kallon da Hajia ke mata, da sauri tace "Hajia kinsan shi da shirmen banza, bai san me yake fad'a ba wani lokacin, komai ya zo bakinshi saiya fad'a." Amna ce ta kalli Ummy ranta a matuk'ar b'ace na marin data wa mijinta, d'an k'aramin iska ta furzar irin na rashin jin dad'in nan kafin ta matsa kusa da Ammar da har yanzu ya k'asa d'agowa, a hankali ta kama hannunshi tana kallonshi, ganin bai kulata ba yasa ta kalli Hajia tace "Hajia dan Allah kiyi hak'uri ki barta anan, wallahi bata san tafiya ita ma." Wani kallo ta mata tace "Ita ta fad'a miki bata so? Ko kin ari bakinta ne kin ci mata albassa?" Kallon Hamna tayi tace "Na sani bata so, kuma gata nan ku tambayeta." Mahaifinsu ne yace "To ko bata so ba dole ta hak'ura ta so ba tunda Hajia tace a tafi da ita." Hajia ce ta kalli Hamna tace "Ke kika fad'a mata ba kya son tafiyar?" Kallon Hajia tayi ta kalli Amna da ita ma ta kafeta da ido, kallon kiyi hak'uri ta mata sannan ta kalli Ummy dake kusa da ita, a k'wayar idon Ummy ta hangi abinda ta kasa fahimta, shin tana son tafiyarta ne ko kuma a'a, rashin sanin amsa yasa ta kalli Hajia ta sunkuyar da kai tace "Ni ban fad'a mata ba, ina so na tafi tare da Abba." Kallon mamaki da takaici Amna ta mata, me yasa za tayi haka? Cikin jin haushi tace "Amma ai ni nasan ba kya son tafiyar, kuma idan kin manta na tuna miki, kina shirye shiryen tafiyarki koyon kwalliya ne." Idan har ba bak'ar magana ta fad'a mata ba tasan ba zata rabu da ita cikin sauk'i ba, dan haka tace "Ni bana son koyon wata kwalliya, wajen mahaifina zan koma da zama." Murmushin rainin hankali Hajia ta bisu da shi tace "To kinji abinda ta fad'a da bakinta, dan haka ki barta ta tafi can, idan da rabo ma ta samu miji acan aure zan mata, sai dai kawai kije bikinta idan da hali." Da k'arfi ya kalleta, *miji*? kuma *aure*? acan d'in? Hummm! Juyawa yayi da sauri ya nufi hanyar barin d'akin, da sauri Amna ba tabi bayanshi dan bata ga abinda zata zauna tayi ba, kai tsaye b'angarensu suka koma. Kallonta Hajia tayi tace "Ki d'auko kayanki ki zo ku wuce." Juyawa tayi ta koma sama, ba b'ata lokaci ta d'auko ta sauko k'asa, tana zuwa Gombo ya mik'e yana wa mutanen wajen sallama, tafiya sula fara yi suna barin falon, anan Ummy ta samu damar fad'awa Hamna cewa "Karki damu Hamna, ki tafi dasu yanzu, tunda Hajia ta yanke hukuncin nan babu mai hanawa, amma ina so duk abinda kike ji a jikinki karki bari kowa ya sani, ki kira ki fad'a min zansan abun yi, kafin lokaci mai tsayi kuma nasan ta hak'ura tasa a dawo dake." Jinjina kai kawai tayi suka fita, a farfajiya daidai k'ofar fita suka samu an saita hancin motocin, anan suka samu Aissata tsaye tana amsa waya da harshen zarma, saida ta gama wayar kafin ta kallesu cike da izza da d'aga kai sama tace "Sai anjima." Zeituna da Zeinabu ne suka amsa da "Sai anjima, Allah ya kiyaye hanya." Mai aikin data taho da ita ce ta bud'e mata k'ofa zata shiga, tsayawa tayi ganin Hamna na shirin shiga motar gabansu ansa jakarta a but d'in motar, da mamaki tace "A'a! Me wannan kuma take yi ne haka? Ina zata je ne?" Mai aikin ce ta girgiza tace alamar bata sani ba ita ma, Gambo ne ya tsaya daga shirin shiga motar yana kallonta yace "Tare zamu tafi da ita." Yamutsa fuska tayi tace "Ban gane tare zamu tafi ba? Tare muka zo da ita ne?" "Umarnin Hajia ne, dole haka za ayi madame." Cewar Zeinabu, rai a b'ace ta juya ta kalli Gambo, kallon kiyi hak'uri mana har muje gidan ya mata, saida ta matse baki alamar akwai magana kafin ta shiga motar, tasan kawai dan Hajia ta muzguna mata ne ta had'a su tafiya da Hamna, amma inba haka ba meye na sawa a tafi da ita, yaran da ko da k'uruciya basu tafi ba bare yanzu da girmansu, suna kallo suka ja motoci suka fita daga gidan anata jiniya, basu zame ko ina ba sai filin jirgi, daga nan kuma suka d'aga zuwa Niamey. D'akinshi ya shiga ya rufe zauna kan gado, tunanin abinda ya faru yake yi, yaji zafi sosai, ba wai marin data masa bane ya b'ata masa rai, marinshi da tayi a gaban wacce zai iya kira da matarshi, ta d'aga hannu ta dalla mishi mari, jin bugun zuciyarshi ya fara canzawa yasa shi mik'ewa da sauri ya fito daga d'akin yana fad'in "Ina! Ba zan tab'a bari damuwarku ta sa min ciwon zuciya ba, idan na mutu ma ba ciwo zakuji ba." Falon ya dawo ya nufi wajen fridge ya bud'a ya d'auki ruwa, saida yasha sosai sannan ya dawo ya zauna kan kujera, tv ya kunna yana kallo sai kuma ya tuna da Amna, tunda ya nufi d'akinshi ita ma tabi bayanshi, amma kallon daya mata yasa ta shiga d'akin ta ita ma. Mik'ewa yayi ya shig d'akin, kwance take kan gado tayi ruf da ciki, k'arasawa yayi ya zauna kusa da ita yana ci gaba da kallonta, sai dai yafi mayar da hankalinshi kan hannunta na hagu wanda ta mik'ar dashi, ta kifa hannun ta mik'e yatsunta wanda ke rufe da jan lalle, amma yatsanta manuniya sai bubbugashi take akan katifar da sauri sauri kamar tana bubbugashi akan tebur, shafa hannun nata yayi hakan yasa ta tashi zaune tana kallonshi, sunkuyar da kanta tayi sanda taji wasu hawaye sun taho mata, da alamar damuwa ya kalleta yace "Kuka ne kike? To me akayi kuma yanzu? Amna bana son kuka fa ko da na yaro ne." Abinda ya fad'a ne yasa ta rushewa da kuka ta d'ora kanta akan kafad'arshi, cikin kuka take fad'in "Yah Ammar bana jin dad'i, zuciyata kamar zata fashe, yer uwata yau tayi nesa dani, sannan Ummy ta mare mijina a gabana, banji dad'i ba ko kad'an, kawai dan babu yanda zanyi ne." Murmushi yayi duk da bata kallon fuskarshi, cikin wata k'asaitacciyar murya yace "Hakan na nufin zaki iya tsayawa sosai akan kare min mutumci na?" D'agowa tayi ta kalli k'wayar idonshi abinda ta jima ba tayi ba tace "Yah Ammar kai fa mijina ne, zan iya yin komai akan kare mutumcinka." Wani murmushin ya kuma yi tare da jawota ya rumgume, shafa yake yi a hankali yana fad'in "Dama na fad'a miki Amna, ina so ki zama farin ciki na da kwanciyar hankali na." Da sauri ta sake d'agowa tace "Zan zama, zan zama yah Ammar, ka kwantar da hankalinka." Sake dawo da ita yayi jikinshi ya sauke k'akk'arfar ajiyar zuciya har iskan bakinshi ya sauka kanta kafin yace "Allah na gode maka, ka bani uwa ta gari da fari yanzu kuma ka ban mata wacce zata kula dani." Ummy na shiga d'akinta Zeituna tabi bayanta, tana shiga ta same ta tsaye tana kai da kawowa da alama hankalinta ba kwance ba, k'arasawa tayi da girmamawa tace "Ummyn Ammar dan Allah zamu iya yin magana idan ba damuwa?" Babu alamar sakin fuska a tare da ita ta tsaya wuri d'aya ta kalleta tace "Ina jinki." Saida ta numfasa ta d'an kalleta tace "Aunty akan abinda ya faru ne yanzun dama, sai nake ganin kamar kinyi saurin marin yah Ammar, shi fa yanzu ba yaro bane, ya mallaki hankalin kanshi sannan yana da iyali, ko kamar Kamal yanzu a wannan zamanin duka baya gyara shi bare kuma kamar yah Ammar, ina ganin zaifi kyau idan kika jawo shi jikinshi, idan kikayi haka zaku fahimce shi da kyau kusan matsalarshi, dan na fahimci daga ke har Alhaji babu wanda yake nuna damuwarsa akan shi, wallahi wani lokacin sai kuyi kamar ba iyayenshi ba." Tunda ta fara maganar Ummy ta rumgume hannaye tana mata wani kallo, saida ta dasa aya cikin mamakin k'arfin halinta tace "Zeituna wacece ke? Meye ruwanki da sabgar data shafi ni da d'ana? Me kike ji dashi da har zaki tare ni da maganar nan? In haifi d'an a ciki na ki nemi ki koya min yanda zan tafiyar da al'amarin daya shafi tsakani na da shi? Akan wane dalili?" Kallonta Zeituna tayi a wannan karan babu wani girmamawa tace "Kawai dai ina so na ankarar dake ne da wuri kafin lokacin nadama ya zo muku, dan n..." Tsawa Ummy ta mata ta hanyar fad'in "Shiru." Shirun tayi tana kallon babu alamar jin tsoro ko makamancin haka, d'orawa tayi da "Bari kiji Zeituna, wannan ba abinda ya shafeki bane, ki fita a harkata tsakanina da yaro na, idan kuma ba haka ba zaki ga wata Sa'ada wacce baki tab'a tunanin zaki santa ba." Girgiza kai tayi tace "Allah ya baki hak'uri, Allah yasa ku gane gaskiya." Tana fad'a ta juya ta bar d'akin, da harara ta bi ta dan dama ranta a b'ace yake, zaune tayi bakin gado ta soma tunanin abunyi na gaba tunda Hajia ta wargaza musu shirinsu. *Zuwa* magrib duk wani bak'o daya zo bikin nan ya koma garinsu, ana sallah magriba lieutenant ya d'auki Zeituna suka tafi ganin kawu Mamu, a k'ofar gidan ya tsaya ita ta shiga ciki da sallama, babu wanda ya amsa sallamarta sai Jumma dake cikin garken awaki da tace "Wake sallama?" Saida ta zagaya inda taji muryarta tace "Inna Jumare nice." Duk da ta d'auki muryarta saida tace "Ke ce wa?" "Zeituna." Ta bata amsa, da sauri ta saki k'afar akuyar da zata d'aure ta taho da sauri tana gyara d'aurin k'irjinta tana fad'in "Yawwa sannu da zuwa, naji dad'in zuwanki, kamar kinsan ina nemanki dama." Tsaye tayi tana kallonta inda ita kuma ta fara masifa cikin fulatanci tana fad'in "Zeituna wane rashin mutumci ne wannan? Daga an aiki yarinya gidanki sai yaron gida ya mareta, me ta mishi to? Kuma ke a gabanki amma babu abinda kikayi, dama had'a baki kukayi dan a ci mutumcinta ko, ke tunda muke dake a gidan nan kin tab'a ganin ni ko ubanta wani ya d'aga hannu ya daketa? Sai wani d'an k'ato kawai kamar ya samu jaka ya marar min yarinya." Masifar da take yi ce tasa kawu Mamu fitowa daga d'aki, yana ganin Zeituna shima ya d'ora tashi masifar har da cewa "To ki fad'a min d'an uban waye shi a gidan? Wallahi sai naje har gidan da kaina na rama mata marinta, ke a gaban uwarshi da ubanshi ma zan rama mata dan ya gane tana da gata, dan ba zai kumbura min fuskar yarinya kuma ya tafi a banza ba." Ita dai kallonsu kawai take, saida kawu ya gama sannan tace "Kawu ya jikin naka? Da sauk'i?" Cike da tijara yace "Wane jiki kuma? Ni dama lafiyata lau, kawai nace ta fad'a miki hakane dan na samu kud'i a hannunki, dan naga baki damu da mu ba tunda kikayi auren nan, yanzu gashi wannan shegen Janu (Jano) yake ko uban wa ya saka ni gaba akan kud'in shi har yana ikrarin cewa zai rufe ni, to ba dole na samu kud'i ko ta halin yaya ba na biyashi kafin ya rufe ni." Cikin rashin jin dad'i tace "Kawu har nawa yake biyanka ne?" "To ni na sani ne? Kawai ba dai ya bani kud'in na karb'a ba a lokacin ina jin dad'in ganinsu, amma dai nasan zasu kai jaka d'ari biyu." D'an zaro ido tayi tace "Kawu d'ari biyu?" Jumma ce tace "Eh, sunyi yawa ne? Ke yanzu a matsayin da kike ai wannan kud'in ba komai bane a wurink." Kallonta tayi cike da damuwa tace "Inna Jumare wallahi bana da wannan kud'in, ina zan samu d'ari biyu ni kuma?" Kallon sama da k'asa ta mata tace "Kiji tsoron Allah Zeituna, dubi kayan jikinki fa, dubi sark'a da d'an kunnen dake jikinki, dubi jakarki ma abar kallo ce, kuma kice baki da wannan kud'in?" "Amma Inna..." Kawu Mamu ne ya katse da fad'in "Ni ban damu da wannan ba, ba lallai sai ke zaki bayar ba ai, ba ga mijinki ba? Ki fad'a masa halin da nake ciki mana, shi da girmanshi da komai zai bari ne a d'aure sirikinshi a garin nan, kawai ki fad'a masa ke dai zaisan abunyi." Iska ta furzar cike da damuwa da halinsu tana tunanin yanda zata fara tambayarsa kud'i masu yawa haka, sai yanzu ta fara nadamar k'in amsar kyautar da yake yawan yi mata lokuta da dama, yakan bata kud'i yace ko zatayi wani abun ba sai ta tambaye shi ba, tunda yer uwarta na zuwa aiki ita kuma bata damu ba, amma sai tace bata so bata buk'atar komai, idan ya matsata sai tace ya rik'e idan ta tashi zata tambaye shi. Yanzu gashi bukatar kud'in ta taso mata sai dai masu yawan da ba zata iya tambayarshi ba, ajiyar zuciya tasauke kallesu tace "Shikenan kawu, zan san abunyi dai." "Da dai yafi." Cewar kawu Mamu, Jumma ce tace "Zeituna wai uban waye ya marar min yarinya?" D'an murmushi Zeituna tayi tace "Inna Jumare d'an shi ne fa." "D'an shi? Kuma shine baki rama mata ba saboda kina so ki nuna mishi ba kya k'aunarta." Wani kallo Zeituna ta mata, na rama mata? Yah Ammar d'in zan mara? Lallai baki san waye shi ba, to ai ko ni har yanzu ban wuce ya galla min mari ba, wayarta ce tayi k'ara ta fito da ita daga jaka, saida ta ga sunan kad'ai ta iya tuna ashe fa tare suke, da sauri ta juyo dan fitowa ta same shi tana fad'in "Na manta ashe yana waje." Kallon juna sukayi inda kawu Mamu yace "Kinji shiririta, tare suke ta baro shi waje." Duk hayaniyar da suke a cikin gidan yana ji, sai dai rabi fulatanci ne rabi kuma hausa, hakanne yasa shi cabko matsalar da suke magana akai, sannan yaji sunan d'an shi ma ya fito da kuma ta'asar da yayi, dan haka ya kirata a waya dan da alama ta manta shi a k'ofar gidan. Tana zuwa ta marairaice tace "Alhaji kayi hak'uri dan Allah na barka k'ofar gida, wallahi su kawu ne suka rik'e ni da magana." Babu alamar wasa a tare dashi yace "Me yake faruwa? waye zai rufe shi akan kud'i? Me kuma ya had'a Ammar da Jumare?" Baki ta saki tana kallonshi da mamaki da kuma rashin jin dad'i, kenan ya ji komai? Oh Allah, cikin taushin murya tace "Ba komai." Kafeta yayi da ido yace "Ya zaki ce ba komai, duk da ban ji komai ba amma ai na fahimci inda zancen ya dosa, fad'a min meke faruwa?" Cike da rangaji tace "Idan mun koma gida zan fad'a maka, amma Abban Ammar ban so kayi hushi." "Shikenan, yanzu ya mai jikin?" Dariya ce ta kubce mata ta rufe baki, dan ya bata dariya sosai data tambaya, hakan na nufin baiji abinda aka fad'a anan ba kam, klonta yayi yace "Meye?" Girgiza kai kawai tayi ba tace komai ba tace "Shigo muje." Girgiza kai yayi da sauri yace "A'a, idan dai zasu iya ki fad'a musu ina waje, in kuma kwance suke kawai ki gaishe min su sai ki fito mu koma." Kamar zata fashe da kuka tace "Lahh, na d'auka fa nan zaka barni da naga mun taho da wuri." Hararanta yayi yace "Lafiya kike? A halin da kike ciki kulawa kike buk'ata, sannan hidimar da akayi duk kin gama wahalar min da kanki da baby na, dan haka ba zan barki ba, ki shiga ki fito mu koma daga baya kya dawo ganinsu." Juyawa tayi ta nufi ciki har da buga k'afafu take tana kukan shagwab'a, da murmushin birgewa ya bita cike da k'aunar yarinyar. Tare suka fito da kawu Mamu suka gaisa sosai, da zai tafi ma wasu kud'in ya sake bashi, babu kunya babu kawaici ya karb'a yana godiya kafin ya koma ciki suma suka tafi. Tun a hanya ya sake tambayarta abinda ke faruwa, tsaf ta fad'a mishi amma banda marin da Ammar ya wa Jumare, dan haka yace "To ita kuma Jumare da waccen ya mareta fa?" Cikin turo baki tace "Jumare fa rashin kunya ta min shine ya hukunta ta." Kallonta yayi yace "Ban gane ba? To shi shi ta wa da zai mareta? Ke fa naga alama kin d'aukeshi wani mutumin arzik'i." Wani kallo ta mishi mai kama da na tsani kalmar daka fad'a, sake kallonta yayi sai yaga ta k'ura mishi ido tana kallo, d'aga mata gira yayi yace "Lafiya?" Had'e rai tayi sosai alamar bata ji dad'i ba tare da kawar da kanta gefe, cikin d'an d'aga murya yace "Wai meye? Wani abu na fad'a daya b'ata miki rai ne?" Juyowa tayi cikin tsananin masifa har ta manta dawa za tayi magana sai ta fara fulatanci tana fad'in "Gaskiya ni na baku kyautawa, d'an da kuka haifa a ciki kuna fad'a mishi duk abinda ya zo bakinku, yanzu meye na wani cewa wai ina ganinshi kamar mutumin arzik'i, to mutumin banza ne dama? Akan me zaka fad'i haka a kanshi?" Tunda ta fara magana ya saki baki yana kallon nata bakin, yanda ko wane harafi ke fita na bakinta abun birgewa, masifa take amma kuma ta mata kyau, sai dai abun takaicin baiji komai data fad'a ba, bakinta kawai ya gani yana motsawa da sautin harrufan da take furtawa, kallon gabanshi yayi yace "Idan kin gama fad'an saiki fad'a min me kika ce ko." Sak'e tayi ta kalleshi, wai dama ba da hausa tayi magana ba? Kawar da kanta kawai tayi ita ma har suka isa gida, katari kam suna shiga sun aje motarsu Ammar shi kuma zai shiga tashi motar, da mutuntawa ta kalli Zeituna yace "Uwa barka, daga pakarey ake?" Murmushi tayi duk da bata san me yake nufi da pakarey d'in ba, kallon lieutenant yayi yace "Alhaji ya ake ciki?" Banza yayi da shi zai wuce Zeituna ta d'an rik'o rigarshi, tsayawa yayi ya juyo ya kalleta da alamar tambayar lafiya, saida tayi kamar zata fad'a jikinshi ta kashe murya sosai tace "Magana fa yake maka, dan Allah ka amsa mishi, laifin me yayi maka?" Cikin fad'a yace "Ke baki ji me yayi bane? Ina ubanshi zai wani ce min ya ake ciki, dallah rabu dani." Fizge rigarshi yayi ya juya zai wuce, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in "Shikenan nagode da abinda ka min." Juyowa yayi yana ganinta ya dawo yana fad'in "Wai ke meye haka? Dan Allah wuce muje." Juyawa tayi ta kalli Ammar daya ke daf da shiga mota sannan ta kalle shi tace "Babu inda zanje yau sai na gani da ido na kuma naji da kunnuwa na ka lokacin da zaka sa mishi albarka, inba haka ba kuma yanzun nan na koma inda muka je yanzun." Yanda tayi maganar ya nuna rigima take ji, sai dai shi a wurin shi ba wani abu bane da ita take kambama shi har haka, turo baki yayi kamar yaro yace "Kira shi to." Take murmushi ya maye gurbin fuskar shanun nan, sam farin ciki yasa ta manta sai ta k'walla kiran sunan Ammar daya shiga mota har ya tayar, bai ji kiran farko ba saida ta kura shi sau uku sannan ya fito daga motar, cike da takon k'asaita ya zo gabansu ya tsaya yana kallonsu. Kallonshi lieutenant yayi babu annuri yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` ✪{T . N}✪📖🖊️ https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl _Bismillahir rahamanir rahim_ _40_ "Ina zaka je yanzu da dare? Baka san yanzu ka girma bane?" Wata yar banzar dariya ya bushe da ita kamar da bakin k'warya, galala Zeituna ke kallonshi inda lieutenant ya nuna mata da yatsa yace " Kin gani? Ina fatan yanzu kin fahimci wani abu." Babu alamar wasa a fuskarta ta kalleshi tace "Tambayar daka mishi ai tana nuna damuwarka ne a kanshi, shi kuma abun ya zo mishi a bazata ne, na tabbata abinda ya bashi dariya kenan, idan kuma baka yarda ba ka tambaye shi kaji." Kallon Ammar yayi da har yanzu ke dariya har da rik'e ciki yace "Dallah ka mana shiru malam." Shirun yayi yana kallonshi, saida ya saisaita nutsuwarsa sannan yace "Zan fita ne Alhaji, asibiti zanje, akwai marasa lafiyan da zan gani nan da minti ashirin." D'an jinjina kai lieutenant yayi alamar gamsuwa tare da cewa "Saika dawo, amma karka cika dare ka bar min 'yata ita kad'ai, kasan har yanzu bak'i ne su." Juyawa yayi bai ce komai zai tafi sai kuma lieutenant yace "Dama ina son ganinka." Dawowa yayi yana fad'in "Gani." Saida ya saci kallon Zeituna kafin yace "Yarinyar da ta zo d'azu gidan nan me yasa ka mareta? Baka san yer uwarta ce ba?" Kallon daya ma Zeituna yasa lieutenant cewa "To ba ita ta fad'a min ba, yanzu daga gidan muke kuma ran iyayenta ya b'ace, har naji mahaifinta na cewa ma zai zo har gidan nan ya rama mata." Wani murmushin yau ga banza ta samu ya ma lieutenant, mayar da kallonshi yayi ga Zeituna yace "Uwa ni kam ina ne gidanku ma?" "Babu nisa da nan ai, kana shiga kwanar..." A firgice lieutenant ya kalleta saboda jin zata kwafsa, shi fa ya fita sanin waye d'anshi, shi ya haifi abinshi, dakatar da ita yayi da cewa "Ke kuma miye haka? Daga ya tambayeki saiki fad'a masa." Kallon ashe ka harbo jirgin ya masa tare da sakin murmushi yace "Abba hak'uri zanje na basu, kace yace zai zo har nan, ku surukai ne bai kamata a samu matsala a tsakaninsu a dalilina ba." Da sauri Zeituna tace "Kwanar beauté salon, a jerin gidan Alhaji Chapi'u cikin bukkokin nan." Murmushi yayi sosai wanda yasa hak'oranshi fitowa saboda jin dad'i, lumshe ido lieutenant yayi alamar shikenan, ta fad'a an gama kuma, juyawa ya sake yi sai kuma Zeituna ta kalli lieutenant kallon dake ankarar dashi bai mishi addua'r ba, yanda ya kalli Ammar yasa shi tsayawa yace "Alhaji kana son wani abu ne?" Saida ya k'ara gimtse fuska sannan ya d'aga mishi hannu alamar ya zo, matsowa yayi kusa da shi a lokacin ya dafa kanshi ba tare daya kalle shi ba yace "Allah ya maka albarka, saika dawo, ka kula da kyau, kada kayi abinda zaka zubar mana da mutumci." D'ago kai yayi ya kalle shi, tabbas dai shine daya sani ya saka mishi albarka, sai dai ba yayi ne saboda ya cancanta ba, baiyi ba saboda ya haife shi, yayi ne saboda an sa shi, jinjina kai yayi alamar to tare da kallon Zeituna, murmushi ya mata na jin dad'in namijin k'ok'arin da tayi yace " Nagode uwa." Kallonshi yayi tare da juyo mishi kumatunshi yace "Ka k'arasa kadarka Abba na." Kallon ban fahimta ba ya mishi yace "Ban gane ba? Me kake nufi?" Kallonshi yayi yace "Sumbata ta zakayi, yaushe rabon da kayi haka dan Allah, ko da muna yara ma baka cika yi ba saboda kai ba mazauni bane." Kallon Zeituna lieutenant yayi ya gimtse fuska, da ido ta masa alamar kayi mana, sake matsowa yayi yace "Abba sauri nake fa." Saida ya rufe ido ya fara matso da fuskarshi kusan tashi, a hankali ya sake bakinshi kan lallausan kumatunshi had'e da k'asumbarshi, a hankali ya sauke mishi sumba mai kyau inda Zeituna taji sautin "Mtsss." Wangale baki tayi tsabar farin ciki kamar an mata albishir da gidan aljanna tace "Weeee, munyi nasara." Kallonshi Ammar yayi ya rik'o hannunshi, yana so yayi magana amma yana jin kamar ba zai iya ba, sai dai daga kallon da yake aika masa zaka fahimci shauk'inshi da kuma kaunar mahaifinshi, sakin hannunshi yayi ya juya zai tafi sai kuma ya tsaya ya juyo, kallonshi yayi yace "Nagode Abba, da ina samun irin haka kullum kaso hamsin na abinda ke zuciyata zai warke." Kallon Zeituna yayi yace "Uwa ce ke mai wuyar samu, uwa mai tsadar gaske." Yana fad'a ya juya barsu nan tsaye, kallon Zeituna yayi yace "To yanzu kinji dad'i." Turo baki tayi gaba ta girgiza tace "Fiye da zatonka."Juyawa tayi da sauri ita ma ta nufi babban falo ta manta da lieutenant tsaye, bin bayanta yayi yana mamakin halinta da yarinta, wato dole indai ka auri yarinya komai tsufanka sai tasa wata rana kayi k'uruciya kai ma. Tun magriba ta shirya tare da Huda tana jiran shigowar Junaid dan yasan abinda ke faruwa, tayi niyya zata zauna anan tare da yarta, idan kuma yace bai yarda ba zata nuna mishi sai dai ta bar gidan, tasan kuma yana sonta ba zai yarda ta bar gidan ba. Bai shigo ba sai bayan sallah isha'i, yana sallama Huda ta tafi a guje ta rumgume shi saboda sabon da sukayi na kwanakin baya, shima rumgumeta yayi cikin farin ciki yana fad'in "Huda ke ce a gidan namu? Yaushe kika zo?" Saida ta d'ago ta kalleshi tace "D'azu muka zo ni da tanti Iklima." Da farin ciki yace "Da kyau, kice ziyara kika kawo mana, amma dai zaki kwanar mana anan ko?" Juyawa tayi ta kalli mahaifiyarta dake tsaye bayansu, k'arasa mik'ewa yayi tsaye shima yana kallonta, kwalliya ce tayi ta d'aukar hankali da fitar hayyaci, k'ananan kaya ne jikinta wanda suka nuna komai, murmushi ta sakar masa tare da matsowa ta rumgume shi, cikin kunne ta rad'a mishi cewa "Sannu da zuwa gwarzona." D'an sumbatar kumatunta yayi tare da cewa "Sannu da gida." Juyawa Huda tayi ta koma kan kujera ta zauna, binta yayi da kallo sannan ya kalli Maryama yace "Amma anan zata kwana ko?" Kama shi tayi suka nufi d'aki tana rik'e da k'ugunshi tace "Eh, ai dama da aka taho da ita ba dan ta koma bane, zata zauna anan ne tare dani, tunda kaga Mama ba lafiya ne da ita ba, Inna kuma girma ya zo ba zata iya kula da ita ba." Sam shi dai baiji wani abu ba a game da zaman Huda anan, sai dai yasan zasu samu matsala da Hajia, haka ma mahaifiyarshi dake da tsegumi, zata ga kamar yarinyar zata gaje shi ne, jin shiru yasa ta lek'a fuskarshi tace "Ya dai? Ko baka amince bane?" Kallonta yayi yace "Haba dai, wacece Huda da har zan kasa amincewa? Ko ba komai fa yarinya na samu a sauk'i." Murmushin jin dad'i tayi ta rumgume shi tace "Nagode gwarzona, Allah ya bar min kai." Tun daga falo sautin kuka ke tashi har zuwa uwar d'akin, yayi rarrashin duniya da ban baki amma ta k'i dainawa, yayi duk yan dubarun daya sani amma maganar d'aya ce har yanzu ita ce "Wallahi zafi, ciwo nake ji, shikenan mutuwa zanyi, ni kawai ka kaini wurin Mama na." Tagumi ya zuba yana kallonta, da farko tausayi take bashi saboda shi kanshi yasan ta aikatu sosai, bai d'auka zata jure wahalar daya bata ba, amma da tafiya ta tafi saita fara bashi haushi saboda ganin kamar da gangan take yi, amma yanzu mamaki kawai take bashi, dan shi dai baiga abun jininin ba. Duk da taga irin kallon da yake mata baisa ta daina kukan ba, har ga Allah zafi take ji ta yanda tana zaune ne kawai saboda kar yaga rakinta yayi yawa, ganin ya k'ura mata ido ya daina rarrashinta ma wanda ke sa ta d'anji dad'i yasa ta k'ara bud'a murya tana murza k'afafu k'asa da yarfa hannaye tana fad'in "Ni kawai ka kaini wajen uwata, Allah ba zan zauna da kai ba yah Jibril, haka kawai duk ka rugurguza ni daga wasa, ni ba zan iya ba ka kaini gida kawai." Cire tagumi yayi ya rufe baki yana dariyar mugunta, lallai yayi babban laifi, domin kuwa daga yan shafe shafe ko da taga zai wuce gona da iri ta fara tsora ta so zille masa, amma saiya kwantar mata da hankali da cewa ai kawai wasa ce yake mata, data tambaye shi da mamaki tace "Wasa fa?" Sai cewa yayi "Eh mana, Hajia ta had'a mu da k'annanmu ba dole mu dinga muku wasa ba." To fa daga nan ne aka yi tazarce ya mata baja-baja, ko da ta lura dariya yake mata saita k'ara himma, cikin dariya ya jawota jikinshi ya rumgume, d'ago kanta yayi ya saita bakinshi cikin kunnenta yace "Yi hak'uri mana 'yar k'anwata, ba zan sake ba daga yau kinji, kukan ya isa haka kar kisa na d'auka ke raguwa ce ba zaki iya dani ba." Da sauri ta mayar da kanta cikin k'irjinshi ta rufe fuska, dariya yayi yana k'ara matseta yace "Kin hak'ura yanzu?" Kai ta d'aga mishi alamar eh, sake matseta yayi ya jingina bayanshi a kujerar yana shafata, cikin saisaita murya yace "Idan Allah ya tashe mu gobe ki tasheni da wuri, dan dole naje na gaishe da kakarku na kuma gode mata data bani ke." D'an d'agowa tayi tace "Kakarmu? Kai fa?" Girgiza kai yayi yace "Jamila ba zan uya da kakarku ba, ku dai kuyita hak'uri da ita wata rana sai labari." Jinjina kai tayi tace "Lallai ma, ai kuwa zanje na fad'a mata abinda ka ce." Murmushi yayi ya sumbaci goshinta yace "Ni ma saina had'ata da hawan jininta." Kallonshi tayi tace "Hawan jininta kuma?" "Eh mana, babban yayanmu ba, Ammar." Murmushi tayi ita ma tace "Allah sarki besty Amna, ko a wani hali take?" Bushewa sukayi da dariya dukansu inda yace "Bana jin a shekara goma zata fahimci mutumin nan." Cikin sanyi jiki Jamila tace "Zuwa lokacin da zata fahimce shi kuma jikinta ya farfashe da duka, zagi kuma tayi buhu buhu har ta fara siyarwa ita ma." Cikin dariya Jibril yace "Bak'ar magana, yab'a magana, gatse, habaici, maganar rashin kunya kuma zasu zama abincinta ne, shiyasa na so Hajia ta had'a shi da kankana, ko ba komai mun daina kallon tv daga ranar, dan kullum da dramar da zamu gani a wajensu." Girgiza kai Jamila tayi tace "Zasu wahalar da junansu ne ai, ita dai bata jin magana, cikin sauk'i ba zai ce ta bari ta bari ba, shi kuma ba nauyin duka yake ji ba, amma kaga Amna tana tsoronshi dama, ko had'a ido bata iya wa dashi, kaga za'a samu sauk'i." "Kema kince wani abu." Ya fad'a yana kallon tvn dake aiki, haka suka ci gaba da hirarsu akan Ammar suna yi suna dariya, a irin hakane har Jibril ya bata labarin wani abu daya faru a shekarun bata da yawo. *A duk cikin labarin nan wannan labarin da Jibril ya bayar shi yafi sani dariya.*😂 Abun ya faru ne shekara d'aya da dawowar Ammar daga Canada, a lokacin ba'a gyara wurin hutawar dake bayan gidan ba, da sassafe ne tashinshi kenan ya zagaya da wayarshi a hannu, yana zuwa ya samu Hamna da Amna suna nishad'unsu bakin bishiya, kamar an koreshi daga sama saiko k'adangaren nan ya fad'o saman hannun Hamna, wanda yanzu haka akwai shatin yagin daya mata, k'wala k'ara tayi ta zabura ta mik'e tsaye ta fara rawar disko a wurin ido rufe tana ihu tana neman a taimaka mata, Amna da ita Allah bai saka mata tsoron wannan abubuwan ba rik'ota tayi jikinta ta buge k'adangaren da shima ya gigice yake neman hanyar barinta, tana bugeshi ya kama gabanshi shima, shiru tayi suna kallon k'adangaren daya bar wurin, daga bayansu Ammar dake ganin komai yace "Shegiyar kankana, ashe sakara ce ke, d'an waccen abun ne kike ma wannan zullon har kina neman cire da siket d'inki." Juyowa sukayi suka kalleshi, turo baki tayi ta harareshi tace "Eh d'in, ina ruwanka?" Dalla mata harara yayi yace "Ke ki kiyaye ni wallahi, ni ne maraininki kenan da zaki juya min d'an banzan baki kamar na tsaka." Murgud'a baki tayi amma ba tace komai ba, juyawa yayi zai bar wurin Hamna ta bishi da harara tace "K'aton wofi, dube shi watak'ila shima tsoronsu yake." Tsaf a kunnenshi, a hankali ya juyo ya fara takowa kansu yana saka wayarshi aljihu, haba ai sai tattare siket tana shirin zabgawa a guje, tako biyu yayi ya fizgota ta dawo baya, rik'e hannunta yayi sosai ya fara kallon bangon wurin yana fad'in "Yanzu zakiyi tsallen mai digri idan ya shiga rigarki ya sosa miki baya." Ko da taji haka ta durk'ushe duk da yana rik'e da hannunta ta fara kuka tana bashi hak'uri, cire slipas d'inshi yayi ya wurga ma wani k'adangare da ya zo wucewa, tip ya fad'o k'asa a mace, janta yayi k'iiii saida ya kaita kusan k'adangaren ya sunkuya ya d'aukeshi da hannu, tana ganin ya d'auka ta k'ara zabga wata k'ara iya k'arfinta, yana nufowa dashi kusanta ta lumshe ido ta lamgab'e tana shirin fad'uwa k'asa, da sauri ya rik'ota yana kallonta, suma tayi da gaske, d'ago idon shi yayi ya kalli Amna dake gefe d'aya ta takure, cikin shan kunu yace "Kawo ruwa." Da gudu ta juya dan kawo ruwan, yana ganin ta tafi ya saki Hamna ta fad'i k'asa da k'arfi, wayar shi ya fiddo ya ci gaba da latsawa, Amna na zuwa jikinta sai rawa yake kamar ita ce ya damk'a, mik'a mishi ruwan tayi ya juyo ya mata wani kallo, har zata bud'e ta zuba mata sai kuma yasa hannu ya karb'a, yana bud'e bakin robar ya shek'a mata su a fuska, a firgice ta mik'e tana sakin yar k'ara, yana ganin ta mik'e ya jefa mata robar ya nufi hanyar fita, Hamna da takaici ya gama kasheta sai cewa tayi "Allah ya isa sojan banza sojan wofi, k'wara da baka zama sojan ba nasan da duk ka harbe kowa, dan ba k'aramin marar imani za ayi ba." Juyowa ya sake yi da sauri ya nufota yana sa wayarshi aljihu, Amna ce tayi saurin cewa "Dan Allah yah Ammar ka..." Bai bari ta fad'a ba ya mata wani jan kallo yace "Kina son kanki da rahama?" Cikin tsoro tace "Ina so yah Ammar, haka kuma ina so wa yar uwata ma, dan Allah ka k'yaleta ba zata k'ara ba." "To ina zuwa." Ya fad'a yana yin kan Hamna data mik'e tsaye tana kakkab'ar kayanta, kamar guguwa, guguwar wacce ta taso a tsakiyar sahara, haka taji ya sunkuceta yayi sama da ita baki d'aya, saida yaje bakin bishiyar daya same su zaune ya tsaya, kamar a tsarin film sai kuwa ya sab'ata a kafad'a ya rik'e bishiyar ya fara takawa yana hawa da ita, zullo take tana k'ara tana kiran sunan Ummy duk da tasan tana asibiti. Amna ma da gudu ta tafi tana fad'in "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri ka sauko da ita." Ita a tunaninta idan ya hau zai sakota ne ta b'are baya kamar yanda yake wayan cewa wata rana saiya b'are mata baya, saida yaji ya hau inda ya mishi sannan ya tsaya ya tallabota ya mata d'aukar jarirai ya azata kan bishiyar, zaunar da ita yayi sannan ya dirko daga kan bishiyar da k'arfi, d'aga kai yayi ya kalleta yace "Dan ubanki kice tak ki gani idan ban sa aka kawo min zaki ba na d'ora shi anan shima, kedai kinsan me zai faru ai." Juyawa yayi zai fita cikin matsanancin kuka harda shashek'a tace "Dan Allah kayi hak'uri boss, wallahi Allah ba zan sake ba na tuba." Hannuwa yasa aljihu ya d'aga kafad'a yace "Kin tab'a ganin boss yayi niyyar shek'e mutum kuma ya hak'ura ya barshi a raye?" Tafiya yayi ya barsu nan sai Amna data fara k'ok'arin taimaka mata ta sauko, amma ita tayi nisa ba zata iya kama hannunta ba bare ta sauko, kallonta tayi tace "Bari na duba a waje na samo wani ya taimaka miki." Fita tayi inda Hamna ta gumtse baki a zuciyarta tana fad'in "Azzalumi mai bak'ar zuciya mugu." Jim kad'an sai ga Amna tare da Jibril da Iya sun shigo, tunda ya ganta saman bishiya ya kece da dariya, saida ya ci mai isarsa kafin yace "Ke kuma me kika mishi haka daya d'oraki kan bishiya?" Shiru ta masa sai kumbura take kafin ya taka da k'yar ya kamo hannunta, saida ya sauko sannan ya k'ara kamata ta k'arasa dirowa, duk gidan babu wanda bai ji abinda ya faru ba, wasu sunyi dariya sosai inda su Ummy kuma suka yi ta masifa da fad'a. *Ci gaba* Zuwa *09:30* na dare ya kammala da majinyatanshi, ban d'akin dake cikin ofishin ya shiga ya fito, wata coffre ya bud'a ya fito da wasu kaya, wandon jikinshi ya fara cirewa ya sauya da wannan sannan ya zauna ya d'aura wannan guma'gumen takalman bak'ak'e, cire riga yayi ya saka wannan ya b'alla botiran ya d'an rage ma hayyanen tsayi ta hanyar nad'esu sannan ya soka rigar cikin wandon, d'amara ya d'aura sosai ya zarge kafin ya d'auki bindiga a cikin gidanta ya mak'alata a wandon, saida ya b'alle buton ya fito da ita ya kalla yayi murmushi ya mayar ya rufe, turare ya d'auka ya fesa sannan ya fito ya rufe ofishin ya d'auko hanyar gida, bai zame ko ina ba sai kwatancen da Zeituna ta masa na gidansu, fitowa yayi a cikin mota ya samu wani ya tambaye shi gidan aka nuna mishi, sallama yayi kawu ya amsa ya fito, yana zuwa ko da suka had'a ido ya d'an dafe cikinshi sakamakon juyawa da yayi, *soja?* Soja a gabanshi? Me yayi zafi haka? Idonshi take suka raina fata jikinshi ya fara rawa, cikin rawar murya yace "Aaaa...bbbb...barka rank...a shi dad'e." Sake zaro mishi ido yayi bai amsa ba sai muzurai yake, k'ara tsorata yayi ya d'an sunkuya kamar zaiyi ruku'i yace "Ranka shi dad'e lafiya? Allah yasa dai ba lafiya nayi ba." Mota ce ta zo wucewa ta haskasu hakan yasa ya ga fuskar Ammar d'in, amma a tunaninshi Amar ne dan shi kad'ai ya sani, ajiyar zuciya ya sauke ya saki jikinshi yace "Sannu ko, Alhaji kana lafiya? Kaine a gidan yau? Ai kuwa yanzu mahaifin naku ma suka bar nan." Baice mishi komai ba sai kallonshi da yake dan haka yace " Ai ban samu damar zuwa d'aurin aurenku saboda bana jin dad'i lokacin, ya hidima kuma?" Wani kallo ya masa yace "Ka sanni ne?" Kallonshi yayi da mamaki, d'an murmusawa yayi yace "Alhaji ai..." Ji yayi kalmomin sun tsaya kuma ya tabbatar bashi ya tsayar dasu ba, hannun da Ammar ya d'ora akan bindigar dake k'ugunsui ce ya tsorata shi, cikin firgita yayi niyyar komawa cikin gidan yana fad'in "To sai anjima." Zai koma ciki Ammar yace "Dakata, ba kaine mahaifin yarinyar nan ba? umm wa take ma? Juuuuu...k'arasa min mana." "Jumare, Jumare, Jumare take, amma ni ban santa ba." Duk yayi maganar ne cikin razani, sake had'e fuska yayi yace "Mu shiga daga ciki mana baba, magana na zo muyi." Ai da sauri ya shiga cikin gidan yace "Taho taho." Saida ya k'ara bud'a k'irji cikin tafiya irinta sojawa masu ji da k'arfi ya bi bayanshi, kawu da jiki ke ta rawa ya tattara yara ya turasu d'aki, Jumma ya ma tsawa yace "Ke baki da wayon kawo tabarma idan kinga mutane?" Tana d'ago kai ta kalli wanda ke bayanshi ta hasken fitilar dake wajen gida da sauri ta tashi ita ma, d'aki ta shiga d'aukar tabarmar amma gabanta da zuciyarta bugawa suke, haka ta d'auko ta shinfid'a musu ta koma d'aki, ba tare daya cire takalmin ba ya zauna a tank'washe k'afafu amma wajen takalmin a k'asa, saida ya d'aga kai ya kalli kowace kusurwa kafin ya kalli kawu dake gefenshi tsaye ya had'e hannaye yana kallon ikon Allah, a kaikaice yace "Fulani ne ku ko?" "Eh Alhaji." Kallonshi yayi ya saki fuska yace "Za'a samu nono?" Kallonshi kawu Mamu yayi, nono kuma? Lallai yau farar rana ce a wurinshi, basu cika aiki da fura da nono ba sosai, amma yau saiya aiki Jumare ta siyo mishi fura da kuma nono mai yawa har da sukari (sugar), da sauri yace "Eh akwai, Alhaji ai ba'a rasa nono a wurin bafulatani." Murmushi ya mishi yace "To a kawo min, sannan a sa sukari." Da sauri ya shiga bukkar Jumma ya sameta, a k'warya yace ta zuba dan watak'ila bafulatani ne shima, dan duk da tsoro bai bari ya mishi kallon tsaf ba yaga sufarshi, yana zuwa ya kawo mishi ya juya zai koma ciki yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` ✪{T . N}✪📖🖊️ https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl _Bismillahir rahamanir rahim_ _41_ "Zauna mana Abba, ai wurinka na zo." Dawowa yayi ya zauna jiki na ci gaba da mishi rawa ya d'an zauna kan turmin dake kwance yana kallon Ammar, saida ya kifa k'waryar nonon nan bakinshi yasha kafin ya sauke ya kalli kawu yace "Abba, Abba na ya fad'a min 'yarka ce na mara d'azu da safe, kuma ya fad'a min ranka ya b'ace sosai har kana cewa ma zaka je ka rama mata, shine na hutar da kai ta hanyar kawo kaina." Zaro mishi ido yayi yace "Ni? Yaushe akayi haka! Allah yaro inaga dai bai fahimce ni bane, ni kam ina ni ina tab'a jikinka yallab'ai." Wani kakkausan kallo ya masa yace "Kana nufin Abba na k'arya ya min kenan?" Da sauri yace "A'a Qur'ani, gaskiya ya fad'a, amma bani na fad'a ba Jumma ce, uwar yarinyar." 😂Jumma na d'aki tana jinsu gatsal tayi daga d'aki ta fito tana fad'in "A'a Baffan Jumare, kaji tsoron Allah fa." Kallonta Ammar yayi, wani irin juya mata kai yayi alamar ta koma ciki kamar maciji, juyawa tayi ta koma tana kallon kawu Mamu, shi kuma binta yayi da fulatanci kafin ya kalki Ammar wanda shima ke kallonshi, saida ya sake kallon bukkokin sannan yace "Ina yarinyar take ne?" "Tana ciki, ai bata jin magana ne." Murmushi ya masa yace "Ko zan iya ganinta?" Da sauri ya mik'e yana fad'in "Ba damuwa, yanzu kuwa." D'akinsu ya shiga ya sameta kwance, murya k'asa k'asa cikin harshensu yace "Kin jawo mana bala'i, to tasoyana nemanki kema, kuma karki kuskura naga kina juya bakin nan ko a b'oye ne, ki barmu mu rabu dashi lafiya dan naga ba mai hankali bane." Fitowa sukayi tare inda ya zauna inda yake ita kuma ta durk'usa k'asa tana kallonshi, wannan mutumin ne, hakan yasa ta k'ara shan jinin jikinta, kallonta yayi yana kurb'an nonon shi yana mata murmushi yace "Jumare ya kike?" A tak'aice ta kalleshi ta kuma yin k'asa da kanta, murmushin gefen labb'a ya mata yace "Jumy." Da sauri ta kalleshi, Jumy kuma? Murmushi tayi saboda sunan ya mata dad'i ita kam, ganin kallon da take masa da murmushi yasa shi cewa "Sunan ya miki dad'i?" Murmushi ta sake yi ta rufe bakinta hakan yasa yace " Kina sona Jumare?" Rufe fuska tayi da hannayenta ta mik'e tsaye ta daka da gudu d'aki, binta yayi da kallo yana murmushin mugunta, dawo da kallonshi yayi kan kawu da shima ke murmushi cike da kunyar yaron, wani murmushin ya sake mishi yace "Idan ta amince ai kaga ni da Abbana duk mun zama surukanka." D'an kawar da kai kawu yayi irin fa shi har ya fara jin kunyarshi ma a matsayin suruki, yana ganin haka ya tab'e baki ya sake kurb'an nononshi, aje k'waryar yayi ya tashi tsaye yace "Abba ni zan tunda kun yafe min." _Yaushe suka ce sun yafe?_ Gyara zaman bindigar nan yayi tare da nufa hanyar fita, bin bayanshi kawu yayi suna kaiwa k'ofar gidan yayi daidai da zuwan Jano, Ammar ya sanshi farin sani, yasan ba mutumin kirki bane, mamakin abinda ya kawo shi gidan yake yi, dan haka ko sallama bai yi wa kawu ba yace "Kai kuma fa?" Kamar yanda ya sanshi haka shi ma ya sanshi dan dukansu matasa ne masu ji da kud'i, babu alamar sakin fuska ya bashi hannu alamar suyi musabaha yana fad'in "K'alau." Bai bashi hannun ba sai kallon kawu da yayi yace "Ka san shi ne?" Jano d'auke idonshi yayi daga kansu yana kallon titi yana murmushi, yasan bala'i ne yake nema dashi kawai, shi kuma bai shirya wujijjiga kanshi ba bare ya biye mishi, kawu kuma da baya so Ammar yasan abinda ke faruwa da k'arfi ya kama hannun Jano suka koma gefe yana waiwayen Ammar dake binsu da tuhumammen kallo, yana kallo kawu ya fito da kudin da lieutenant ya bashi ya damk'awa Jano yana fad'in "Gashi malam, na biyaka dan Allah ka shafa min lafiya yanzu, karka sake zuwa gidan nan." Wani kallo ya mishi yana yatsina fuska yace "Ko saboda waccen ne ka hana min 'yar taka? To ka sani waccen babu abinda zaiyi da ita wallahi, kawai zai yaudareta ne sannan ya mayar maka da ita sunan da zaka gagara kiranta dashi." Wani kallon kai kauce kawu ya mishi yace "Kai dallah, ana babbakar giwa wa yake jiyo k'aurin zomo, ai 'yata tafi k'arfin dukanku wallahi, sai dai uban waccen d'in." Wata dariya Jano yasa yana fad'in "Babban arne kenan." Ammar dake cike da shakku matsowa yayi wurinsu ya kalli kawu rai a b'ace yace "Me yake faruwa ne tsakaninka da shi? Kasan waye wannan kuwa? Ba mutumin kirki bane." Wani kallo Jano ya mishi yace "Ammar, ka sanni na sanka, karka shiga sabgata mana tunda bansa da kai ba, kayi abinda ya kawoka nayi abinda ya kawo ni." Daf dashi ya matsa yana fad'in "Ba zanyi sabgar tawa ba Jano kayi abinda za kayi, kai ka sanni wallahi ba zan lamunci iskancin nan daga gareka ba." K'asa da sama ya kalleshi yace "Bana jin rigima, kai kuma kullum a cikinta kake kamar wanda aka haifa ana dabbatuwa, dan haka banda lok..." Bai yarda ya k'arasa fad'a ba ya kai mishi bugu a baki, baya baya yayi ya kaiwa motarshi karo ya dafeta yana kuma dafe da bakinshi, idonshi jawur sukayi har da k'wallar wahala, da sauri kawu ya shiga tsakani yana bawa Ammar baki ya rabu dashi, cikin jin bala'i da masifa yake nuna kanshi yana fad'in "Ni d'in? Ni ne aka haifa kamar ana dambe? To bani ne ba sai dai in kaine ubanka ya haifa yana dambe." Tasowa Jano yayi yana tofar da yawun bakinshi da yake jin sunyi gishiri alamar jini yace "Ni ka wa haka Ammar? Ni? Tak'amarka akwai iko da masu saka kakia gidanku? To wallahi sai kayi nadamar dukan nan daka min, in kuma bansa kayi dana sanin haihuwarka ba to kace ba d'an halak bane ni." Cikin d'aga sauti ya fara fad'in "Yeeee, kai ba d'an halak bane, da gani ma ai ana ganewa, banza mata-maza kawai, ashe k'aramin d'an jagaliya ne kai, to kaji da kyau Jano, ba boka babu malam babu d'an bori, kuma a haka zan ci uwarka, ruwan randa kawai zansha na ma iskancin da baka tsammani, idan har kuka gagara kai da matsafan naka to ka nemi lambata a wurin wanda ya sani, ka zab'i rana da lokacin da zamu had'u da kai a bayan gari saika sa min hannu, watak'ila ka iya huce haushinka ta hanyar rama dukanka." Juyawa yayi ya kama murfin motarshi ya bud'a zai shiga, tsaya yayi ya kalleshi da kyau ya d'aga mishi yatsarshi ta tsakiya wacce tafi tsawo tana kallon sama, sannan yayi alama da yatsunshi cewa sai sun had'u shiga yayi ya tayar ya wuce. Suna had'a ido kawu ya sunkuyar da kanshi yana murmushin mugunta, a ranshi yana fad'in "Ashe kowa da wanda ya raina." Tsaki yayi ya juya a fusace shima ya bar wurin, Ammar ma daga nan asibiti ya sake komawa, wannan kayan ya cire dan baya so kowa na gida yasan shi dasu ya mayar da nashi kafin ya sake komawa gida. Jano na barin nan ya so ya zarce ofishin yan sanda, ba wai dan ya dake shi sai dan ganinshi da kakin soja da yasan ba soja bane kuma yake sawa, yasan inhar doka ce ya taka ta hanyar sa kayan dole hukunci zai hau kanshi, amma saiya bari har safiya tayi sai yayi k'ararshi. Ammar kuma na ko da yaje gida kai tsaye wajen amaryarshi ya nufa, tana zaune kan kujera tana kallo ya same ta, tsaye yayi ya bud'e mata hannayenshi alamar ta rumgume shi, bata fahimce shi ba sai cewa da tayi "Sannu da zuwa yah Ammar." Mik'ewa tayi ta nufe shi tana k'ara fad'ad'a murmushinta, tana zuwa ta tsaya bata matsa kusa dashi ba, saida ya mata kallon zan ci... kafin ya fizgota da k'arfi ta fad'a jikinshi, saida zaman d'an kwalinta ya canza inda tayi fiki'fiki da idonta, matseta yayi sosai yana sauke numfashi, d'agata yayi daga jikinshi ya kalleta yace "Daga yau kika ga na shigo haka zaki min, kuma ko gaban waye ban yarda ki nuna jin kunya ba, haka nake so kuma dole kiyi." Yana fad'a ya wuce ya barta tsaye, juyawa tayi da baki bud'e ta bishi da kallo, d'aga ido tayi sama tace "Allah gani gare ka, ka shirya min bawan nan naka." Zaune ta koma tayi tana ci gaba da kallo, amma duk in taji motsi daga d'akinshi sai gabanta ya fad'i, ana haka dai har ya fito sanye da farin wando iya gwiwa mai aljihu da farar singlet d'in data kama shi sosai, yana zuwa ya zauna kamar zai fad'a mata yana fad'in "Kiyi hak'uri ba zan iya yi miki kwalliya ba, yunwa nake ji kuma na gaji, amma ki sani ni makwoyin sunnar annabi ne." Dariya tayi ta mik'e tsaye ta nufi teburin abinci, da kallo ya bi manyan kayan dake birge shi tare da ayyana luguden da zasu sha yau a hannunshi, cije leb'en k'asa yayi yana lumshe ido, yana kallo ta d'auko kwanukan abinci ta juyo tana takowa, nan ma ido ya k'ura mata yana kallon komai na hallitarta, bai sani ba ko dan komai nasu iri d'aya ne da kankana, ko kuma dan suna da k'ira da hallita irin yanda yake son mace, dan shi dai yafi son mace mai cika hannu yar dumul dumul, ko gajera ce yana sonta a haka bare kuma su dake da tsayi, sannan ga kyawun fuska masha Allah, haka kuma Amna tafi kyau akan kankanarshi, kawai dai haske kankana tafi waccen, shi dai kawai yasan komai nasu yana birgeshi, tana zuwa ta sunkuya ta aje kayan ta durk'usa ta fara zuba mishi, kallon fuskarta yake yace "Amna yanzu ma abincin kika dafa?" Ba tare data d'ago ba tace "Yah Ammar idan ban dafa ba to me zaka ci?" Yatsina fuska yayi yace "Da gaskiyarki kuma, dan kinga banyi tunanin siyo abinci ba." D'an murmushi kawai tayi tare da kallonshi tace "Na aje maka anan ne?" Kai kawai ya d'aga mata, gyara wurin tayi sannan ta aje mishi ta zaune yanda suke fuskantar juna, kallonshi ta sake yi tace "Bismillah." Saukewa yayi ya tank'washe k'afafu yana fad'in "Amma ko baki dafa ba ai ga Hajiarmu, sai muje mu ci na su." Shiru tayi ita dai ko kallonshi ba tayi ba, loma ya fara kaiwa tare da bismillah, saida ya tauna ya had'iye ya kalleta kamar mai karanta wani abu a fuskarta kafin yace "Kinyi kyau sosai." Sunkuyar da kai ta sake yi tace "Nagode." Da mamaki ya kalleta yace "Ke ba zaki ci ba?" Kallonshi tayi tace "Ka fara ci ka k'oshi." Tab'e baki yayi ya jawota ya zaunar da ita kan d'aya cinyarshi, k'ara sunkuyar da kai tayi tana sissinewa kamar ta shige k'asa, d'ebo abincin yayi ya kai mata a baki tana fad'in "Gani ni k'aton banza kenan, na zauna ina cin abinci ke kina kallo na." Tun tana gocewa har ta fara karb'a ita ma, bai barta ba saida ta shagwab'e fuska tace "Wallahi yah Ammar na k'oshi, cikina kamar zai fashe." Kallon rainin hankali ya mata yace "Wannan d'an abincin da kika ci ne zai fasa miki ciki? To gidan ubanwa kika kwaso wannan k'ibar?" Tab'e fuska tayi kamar za tayi kuka a zuciyarta tace "Ai ba kowace k'iba ta cin abinci ba, kuma ubana ba siriri bane bare kace banda inda na gadota." Saida ya shafa cikinta kad'ai ya daina bata ya ci gabada ci har ya k'oshi sannan yayi hamdala, tashi tayi ta d'auke kwanukan ta dawo ta zauna k'asa dan har yanzu shima bai tashi ba, d'aga k'afafunta tayi ta d'ora hannayenta saman gwiwan, bata ankara ba taji ya finciko k'afafunta ya mik'ar dasu, tana kallo ya d'ora kanshi ya juyo da kanshi yana kallon fuskarta, zagaya hannunshi yayi ta bayanta ya d'an zage zip d'in rigarta, d'aya hannun kuma ya zura shi ta cikin rigarta yana wasa da cibiyarta, sam bata yarda sun had'a ido ba sai kawar da kai take yi, abun kamar wasa saiya d'aga rigarta ya zura harshenshi a cibiyarta yana ta karkad'a shi idonshi rufe kamar mai bacci, ita kanta baccin taji yana son figarta ga tsikar jikinta da take mugun tashi, jikinta duk yayi sanyi k'alau d'an d'aya hannun ma bayanta ya zura shi har ya b'alle mata bras data saka wanda dama take jin ta dameta saboda rashin sabo, a hankali ya fara zarmewa ta hanyar zamar da rigarta ya cire mata hannayen, ita kanta bras cireta yayi ya cilla gefe, da sauri ta jawo rigarta zata mayar ya bud'a idonshi da suka bata tsoro saboda canzawar da sukayi, tashi yayi tsaye tare da kama hannunta ya nufi d'akinshi da ita, tunda ta ga inda suka nufa take addu'a a zuciyarta wanda bata ma san me take karantawa ba, tsabar yanda zuciyarta ke bugawa da kakkarwa da jikinta ya fara yi yasa hawaye fara zubo mata, yau kam babu tsumi babu dubara ta shiga hannu kenan. *Wani* k'akk'arfan nishi ta sauke mai tafiya da numfashi, hannayenta gaba d'aya ta luma kan damatsanshi wanda yasa faratunta shigewa sosai a damtsen shi, idonta rufe suke ruf sai kai da take girgizawa hawaye na fitowa a idonta suna bi ta bayan kunne, Inna lillahiwa'inna ilaihi raju'un da kalmar shahada ne a bakinta, zafi ne mai tafiya da k'walwa, lokaci d'aya taji shigar abinda ba tayi tsammani ba, abu ne da bata isa ta kwatanta girmansa ba, ita dai tasan a lokacin daya shiga ne ruhinta ya bar gangar jikinta, mamakinta d'aya shine yanda akayi take motsi bayan kuma tasan gawa bata motsawa. Babu alamar raguwa sai k'aruwa da rad'ad'in keyi, dan haka ta sake lik'e idonta sosai ta cije leb'enta na k'asa tana jan hannunta kan damtsenshi, hakanne yayi sanadiyar fitar da jini daga damtsenshi saboda kaifin akaifunta masu d'an tsayi saboda gyaran da aka musu saboda bikin, tumurmusa kanta kawai takeyi tsakiyar tattausan pillown, inda take ta yin sama tana son zamewa amma sai k'ara lik'e mata yake. Duk abinda ke faruwa bai sani ba, abinda ke zautar da tunaninshi kawai yake son yaji ya samu sauk'inshi, amma abun ya ci tura sai k'ara lik'ewa yar mutane yake, ba ita ba da a jikinta suke shi kanshi da yake tsutsarsu har bakinshi yayi zafi, ya gyara kwanciyar yafi kala hud'u duk dan yana so ya hutar da ita, amma ya jarabar ta k'i kwantawa, a daidai lokacin da yaji zafin yaginshi da tayi a lokacin yayi wata zabura ya sake k'amk'ameta yana wani jijjiga yana k'ara shiga jikinta, daga haka kuma sai yayi sanyi zufa ta keto mishi lokaci d'aya, gefenta ya fad'a yayi ruf da ciki yana sauke numfashin samun nutsuwa, ya jila haka kafin ya iya d'aga kanshi ya kalleta, ganin kanta na kallon gefe d'aya yasa hannu ya juyo da ita, murmushi ya saki ganin har yanzu idonta rufe suke, yunk'urawa yayi ya sauka daga kan gadon ya d'auki gajeran wandonshi ya mayar ya shiga ban d'aki. Zaune ta mik'e tana cije leb'e, saida taji ta wartsake kafin ta tashi ta d'auki kayanta tayi saurin barin d'akin kafin ya fito, tana zuwa d'akinta ban d'aki ta shiga ta saka rigar wanka sannan ta fito, madafa ta shiga ta dafa ruwan zafi masu yawa kafin ta juye a bokiti ta shiga dasu d'aki, tana shirin shiga ban d'aki taji ya shigo d'akin, garin saurin shigewa ban d'akin yasa bokitin ya bugi k'ofar ban d'akin ruwan suka zuba a k'afarta, sakin bokitin tayi tare da sakin k'ara lokaci d'ayakuma take furta Inna lillahi wa'innailaihi raju'un, da gudu ya k'araso ya fitoda ita yana kallon fuskarta cikin fad'a yace "Meye haka? Kina haukane? Wa yace ki fito daga can?" Hijabinta tasa tana goge hawaye, tausayinta ne yasa shi rumgumeta yana shafata yace "Yi hak'uri to, amma me yasa kika taso? Ba zaki iya kula da kanki ba, ko baki yarda dani bane?" Girgiza kai tayi dan haka ya kama hannunta suka shiga ban d'akin, da kanshi ya had'a mata ruwan ya kalleta yace "Zaki iya ko na taimaka miki?" Girgiza kai tayi alamar a'a, barinta yayi ta gyara kanta tsawon lokaci kafin ta kammala ta fito, kwantar da ita yayi yaja mata bargo, kallon fuskarta yayi yana murmushi mai tsadar gaske yace "... *Comment* *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` ✪{T . N}✪📖🖊️ https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl _Bismillahir rahamanir rahim_ _42_ "Nagode, aljannata." Murmushi ta masa mai tafiya da imanin mutum kafin ta fara lumshe ido, sumbatar goshinta yayi tare da gyara mata bargon sannan ya kwanta gefenta, bata jima ba bacci yayi awon gaba da ita, amma shi bai samu damar yin baccin ba sai durmiya da yayi tunanin rayuwa a sanda yake wanke zanin gadon da yaji matsa shi kanshi, yana wankin yana tunanin waccen ranar ma da halak d'inshi ce da shi zai wanke zanin nan, amma baisan waya wanke ba tsabar masifa. Yasan da babbar matsala a gaba idan asirin abinda ya aikata ya fito, amma a shirye yake da duk wanda zai tuhume shi, yana da hujjjojin kare kanshi ko da ba'a gamsu ba. Ko ya take? Ita ce tambayar daya ma kanshi, nan ma zurfafa tunani yayi sai yaga watak'ila tafiyartata zama alkairi a gare shi, tunda ya auri k'anwarta, hakan zaisa ya mayar da hankalinshi kan matarshi. Amma me yasa Ummy ta shiga firgici sosai daga yana son duba kankana? Me yasa daya anbaci ciki duk suka rud'e kamar dai cikin ne da ita? Akwai wani abu! Shine abinda zuciyarshi ta fad'a masa, da wannan tunanin bacci b'arawo yayi gaba dashi. Tun *08:00* na safe colonel ya gama haramar tafiya shi da yaranshi masu tsaron lafiyarsa, yayi sallama da kowa sannan ya fito, a lokacin Ammar ya zo sukayi sallama, colonel zai shiga mota mai gadi ya taho da sauri ya gaishe shi, amsawa yayi kafin ya mik'e daga rusunawar da yayi ya bawa Ammar wata takarda yana fad'in "Wannan wani ne ya bayar yace a baka." Karb'a yayi ya bud'e ya fara karantawa ba tare da yace mishi komai ba, wani shegen murmushi ya saki kamar an bashi katin shiga aljanna, ganin haka yasa colonel tsayawa yace "Yaro na ya dai? Lafiya ko?" Ba tare daya daina wannan murmushin ba ya kalleshi yace "Lafiya lau tonton, wani k'aramin d'an daba ne zai min iskanci, amma zan nuna mishi na fishi iya buru'uba." Yana fad'a ya tunkari hanyar komawa b'angaren shi yana fad'in "Za muyi waya tonton." Cike da bala'i colonel yace "Da kyau yaro, karka ragamar duk uban da yace zai taka ka, a shirye muke muyi shari'a da uban ko waye, kaje Allah ya tsare." *Da sannu halin kowa zai fito* Yana shiga d'akinshi ya wuce ya d'auko makulin mota da wayarshi ya fito, ba dan ta fito daga d'akin ba a lokacin da ba zata san fitarshi ba, amma yana ganinta saiya jawota jikinshi yana kallon fuskarta yace "Matarmu zan fita, ki kula da kanki sannan ki ci abinci idan kin dafa, karki saka dani kuma karki jirani, ba zan dawo da wuri ba." Tsoro ne ya fara bayyana a fuskarta tace "Lafiya yah Ammar? Ina zaka je?" Shafa kumatunta yayi yace "Ba komai, zan dawo amma ba da wuri ba." Yana fad'a ya saketa ya tunkari k'ofa kamar zai tashi sama, da kallo ta bishi sai gabanta da taji yana d'an fad'uwa, ba komai ta gani a idonshi ba sai bala'i, tana jin tsoron amsa gayyatar katin masifa ne yayi daga gurin wani, ita kam ina zata saka kanta da tashin hankalin bawan Allahn nan? K'arasawa tayi ta zauna kan kujera ta zuba tagumin zaman jiran tsammani. Jikinshi har rawa yake ya matsu ko ya isa ofishin, tunda ya cije leb'e ya kasa sakinshi sai k'yaci da yake yafi dubu, to wai shi Jano zaiyi k'ara? To ai ya ma raina masa hankali da baiyi k'ararshi wajen sojawa ba ko jendarme, sai wajen masu saka kakin police, jar uba! Da wannan bala'in ya isa wurin har gaban inspecteur d'in daya shirya sulhunta tsakaninsu da kanshi, dan baya so rikicin yayi girman da sunan gidan Gaga zai b'ace. Daga zaman rashin mutumcin da yayi kamar zaiyi kwance a kujerar tare da d'ora k'afar dama a ta hagu yana kallon kowa da wutsiyar ido zaka san babu arzik'i, kuma k'irirs yake jira ya ta fara zazzage kwandon bala'in daya d'ebo, inspecteur d'in ne ya kalle shi yace "Malam Ammar, wannan ya shigar da k'ararka akan dukan daka mishi, sannan akwai tuhuma da ake maka ta cewa kana anfani da kakin soja alhalin kai ba soja bane, shin me zaka ce a game da hakan?" Saida yayi murmushi yasa babbar yatsarshi a baki sannan yace "Idan shi wannan mahaukaci ne ai ku da hankalinku, a ina kayan suke? Wurin wa ya gani?" Kallonshi Jano yayi yace "K'arya zan maka, kai kasan baka isa ba wallahi." Da k'arfi ya taso daga kwanciyar da yayi kan kujera ya nuna inpecteur d'in yace "Yallab'ai da kai nake magana, ka fad'a mishi karya sake saka min bakinshi, inba haka zan zubar mishi da hak'ora kuma a gabanka wallahi." Kallon Jano inspecteur d'in yayi da ido ya mishi alamar yayi shiru sannan ya kalli Ammar yace "Malam Ammar, ya fad'a mana ba kawai kakin ne jikinka ba har da bindiga, rik'e bindiga baga jami'in tsaro ko kuma wanda ke son kare kanshi ba shi ma saida lasisi babban barazana ce a cikin al'umma, taka doka ne da idan aka kama mutum za'a hukuntashi, amma idan kana da lasisi da takardar izinin rik'eta saika nuna mana hujja, idan babu zamu iya mik'a al'amarin gurin su sojawan sai suji da kai." Saida ya d'an buga teburin gabansu yace "Da kyau, haka nake so ai dama, so nake muje wurin manyanku ta yanda za'a bi min hakk'ina na k'azafin daya min, yace wai ina saka kayan soja, to ni mahaukaci ne ko me? Dan ina son zama soja bashi ke nuna zan uya anfani da kayan ba na firgita mutane, dan haka idan har aka tabbatar k'arya ya min ni kuma zan shigar da k'ararshi na cewa da yayi na saka." Kallonshi inspecteur d'in keyi da mamaki, bala'i da d'umu d'uminshi, Kai ba zan iya ba wannan har ni yasa cikin rigimar, dan haka yace "To shikenan munji, yanzu akan dukan daka mishi a baki har ya fito da jini, anci tararka ta 15 000." Wata harara ya dalla ma Jano yace "Matsiyaci, ai da bara ka koma." Kallon insp. d'in yayi yace "Yallab'ai, gaskiya bana da kud'i, kawai muje mataki na gaba." 😂 _Sis a haka kike son shi ko?_ Wani kallo Jano ya mishi ya d'an saci kallon wandonshi daya kama shi sosai har ana ganin shatin wayarshi da alamun kud'i, amma wai baya da kud'i. D'aure fuska insp. yayi yace "Malam Ammar, muna son sulhunta matsalar nan ne ta yanda ran kowa ba zai b'ace ba, ka biya wannan kud'in ku bawa juna hak'uri tare da alk'awarin kiyaye gaba, shikenan kowa ya tafiyarshi." Zaman farko ya sake yi ba alamar wasa yace "Da gaske na ke fad'a maka banda kud'i, meya kamata nayi?" "Sai mu rufe ka, idan aka zo belinka sai a biya tarar." Ya fad'a ba alamar wargi, murmushi ya masa yace "Bismillah to, ina so dama na shiga ciki na kwana ko d'aya ne, dan bana so har zamani na ya k'are a tarihi na ace ban shiga gidan maza ba." Insp. d'in ne yace "To ai idan kana son shiga gidan mazan na k'warai sai kayi babban laifin da zaka shiga hannun mazan." Kallonshi yayi yana murmushi yace "Indai nine ai zan aikata wata rana, zaka gani a jarida ma." Wurga ido yayi irin kai ta shafa kafin ya kira wani cop yace ya shiga da shi ciki, saida aka karb'e komai na shi kafin ya iza k'eyarshi gaba, saida ya juyo ya kalli Jano yace "Tsinanne kawai, ai zan fito ne karka bari mu had'u da kai, sakarai mata-maza." Juyawa yayi ya kalli insp. yace "Kar a kashe min waya ta saboda masoya na zasu iya kira na a kowane lokaci." Har ya bud'e baki zai mishi magana sai kuma ya zura kai ya tafiyarshi dole ya k'yale shi, yau kam shi ya ga tijaja, shi in ba masu shan k'waya ba bai tab'a had'uwa da irin wannan mutanen ba, kallon Jano yayi ya bashi hak'uri tare da cewa idan anyi belinshi zasu nemeshi dan a musu tsakani, godiya ya mishi ya tafi shi kanshi zuciyarshi ta cika fal da tsoron sake had'uwa dashi d'in, dan yana da tabbacin Ammar da d'an ta'adda ne to ba zaiji wuyar yin k'unar bak'in wake ba, dan shi wani lokacin tsabar bala'i kawai a mutu ko ayi rai ne, ya kashe ko a kashe shi. Ko da aka shigar dashi aka rufe akwai mutane a ciki, wani saurayin mashayi ne ya matso kusanshi yana mishi kallon raini da wani d'aukar kai, a hankali saiya zauna kusanshi irin yana neman masifar nan (kunsan dai a gidan yari kowa yana so yaga ya cuci na k'asa dashi, kuma kowa yana ma kowa kallon k'aramin d'an iska ne), har yanzu bai daina mishi wannan kallon kad'an nake jira ba, Ammar dake zaune kan bancin ya dafe hannayenshi a gwiwanshi yana ta bubbuga k'afa, Jano Jano Jano Jano, sunan da yake ta fad'a kenan ko tsagaitawa babu, jin wannan saurayin na matse mishi wuri yasa shi d'an kallonshi, ganin wannan kallon rashin mutumcin da yake masa irin shi wai shak'iyi ne yasa shi yin murmushin gefen labb'a ya jinjina kai, saida ya sake kallonshi da kyau yace "Meya shigo da kai nan?" Cike da gadara yace "K'waya, ni mai siyar da k'waya ne." Ba tare daya daina kallonshi ba yace "Wa ka tab'a kashewa a harkar taka?" A d'an tsorace ya kalleshi yace "Kisa kuma? Ban tab'a ba." Jinjina kai yayi yana d'auke idonshi daga kanshi yace "To karka shiga harkata, inba haka ba a filin wurin nan zan rataye ka." K'wafa yayi tare da mayar da kallonshi gabanshi, matsawa nesa dashi yayi yana kallonshi yace "Kai ka tab'a kashe mutum ne?" "Sosai ma." Ya fad'a ba tare daya kalleshi ba, da mamakinshi yace "Wa ka tab'a kashewa? Kuma meye sana'arka?" A hassale ya kalleshi yace "Kai, kai zan fara kashewa yanzu idan ka sake min magana, shege kai jarababbe." Saida ya zabura saboda d'aga muryar da yayi, tashi yayi daga wurin gaba d'aya yana kallonshi. A tare suka shiga yau dan gaishe da iyayensu, sai dai yau babu Hajia zaune a kujerar mulki, kai tsaye d'akin mahaifiyarshi suka nufa da sallama, daga ciki ta amsa tare da musu izinin shiga, suna danna kai cikin d'akin ko da ta gansu tare da Huda saita b'ata rai tana musu wani kallo, durk'usawa sukayi dukansu suna gaishe ta, a wani basarwa ta amsa kafin ta kalli Huda data sha shirinta tsaf tace "Yaushe kika zo? Da safen nan?" Junaid ne yace "A'a Mama, tun jiya ta zo ai, yarinyar bata da hayaniya ne shiyasa baki san ta zo ba." Cike da dakiya tace "Uhum! Ta zo ta kwana biyu ne kenan?" Kallon kallo sukayi sai Maryama ce tace "A'a Mama, na sa a kawo min ita ne ta zauna tare dani." "Ban gane ba? Kina so ki ce zata zauna a gidan nan din-din-din?" Saida ta kalleta dan son gano yanayinta tace "Eh." Fuska a d'aure tace "To naji, ki bamu wuri zanyi magana da d'ana." Murmushi Maryama tayi ta mik'e rik'e da hannun Huda suka fita, suna bada baya ta balbale shi da masifa akan me zai yarda ta zo da yarta, ai ba haka akayi da ita ba, a k'arshe ma cewa tayi "Wai kai baka da zuciya ne? Matarka ta zo da 'yar da ba kai ka haifeta ba a gidanka, me zai hana ta kaita wajen dangin ubanta? Ko kuma a cikin karuwan nata bata san waya mata cikin 'yar ba?" A d'an k'ufule yace "Mama, haba Mama, wannan wace irin magana ce? Ni na amince ta zauna damu, wacece Huda? Duk hidimar da zan mata ba zata kai wacce zan yi wa 'ya'yana ba idan na haifa, kawai ki bar maganar nan bana so." Mik'ewa tayi tace "To kaji da kyau, wallahi ban yarda da zamanta a gidan nan ba, kuma kasan Hajia ma ba zata yarda ba, dan haka kafin ta muku wankin babban bargo ka gaggauta fitar da ita a gidan nan, idan ba haka ba babu ruwana duk sanda ta zo cin mutumcinka." "Indai hakane to ni kawai zan koma gida na, dama ban so zama anan ba kawai Alhaji ne yasa na zauna." Fita yayi daga d'akin ya barta tana bambami, yasan za ayi haka dama shiyasa ya shirya juya, a farfajiyar gidan ya sameta nan ya mata sallama ya fita, gidansu ta koma amma madadin ta shiga wurinta saita wuce b'angaren da bata da masaniya ko na waye, saida ta shiga da sallama a k'ofar d'akin suka ci karo da Amar zai fita, gaisawa sukayi a mutumce ya wuce, saida taga fitarshi saita wuce b'angare na gaba dan ba Umaimah take son gani ba, anan tayi sa'ar samun Jibril ko fita baiyi ba, ganinsu yasa Jamila saka hijabi akan k'ananan kayanta suka gaisa, suna zaune ya fito da alama tashinshi kenan, Huda na ganinshi ta ruga ta rumgume shi tana fad'in "Lahhh Abba, ina kwana." Rintse ido yayi tare da gumtse baki yace "Shit!" A zahiri kuma bud'a ido yayi ya mata dariya ya rik'e hannunta yace "Yah beby Huda, ya kike? Yaushe kika zo gidanmu? Kin zo wajen mamanki?" Da fari fad'uwa gabanta yayi jin yarinyar ta kirashi Abba daga ganinshi, amma yanzu tana son sanin dalilin da yasa ta kira shi da haka, kafesu tayi da ido tana kallo, har suka k'araso ya zauna nesa da ita Huda na mishi magana, a kaikaice ya kalleta yace "Madame ya kike?" Wani shed'anin kallo ne take masa wanda bai dace ba, saida tayi murmushi tace "Lafiya lau Abban Huda, ka tashi lafiya?" Saida ya d'an rarraba ido yace "Lafiya lau, ina mutumin ko har ya fita?" "Ya fita." Ta fad'a tana kafeshi da ido, ganin ba zai juri wannan kallon ba yasa shi sakin Huda ya mik'e zai koma ciki, da sauri Maryama tace "Abban Huda nace ko zamu iya magana?" Yawu ya had'e da k'arfi sannan ya juyo ya kalleta, Jamila ma da baki sake take kallonsu, cikin dai k'warewa ta bariki ta mishi alama da kai da ido cewa su fita waje mana, mik'ewa tayi tana rik'e da hannun Huda ta fita, bayansu ya bi jiki a sab'ule yana kallon yanayin yar matarshi wacce ke jin kamar ta shekara a soyayyar mijinta duk ta fara zufa, suna fita k'ofar d'akin ya tsaya ya rufe yace "Lafiya? Me kikeyi haka Maryama?" Da yatsa ta nuna shi tace"Dakata malam, dama dan na fad'a maka Huda ta dawo nan da zama ne, ba wai dan mahaifiyarta na aure nan ba, a'a sai dan nan gidan ubanta ne, gidan da ko babu ni a raye nan ne yafi dacewa data rayu, dan haka ka fara shirya nuna mata gata ita ma tasan 'ya ce." Juyawa tayi zasu wuce sai kuma ta tsaya ta kalleshi tace "Anjima zan bata ta kawo maka takardar haihuwarta, ina buk'atar ka canza mata makaranta ita ma, ya rage naka ka samar mata dreba ko kuma ka kaita da kanka ko ma ta tafi a k'afa duk matsalarka ce." Wucewa sukayi ta barshi tsaye kamar zai kashe kanshi, wane bala'in ne kuma wannan ke shirin danno mishi kai? A haka ya dawo d'akin Jamila na gyara teburin cin abinci, ta baya ya rumgumeta yana shinshinar wuyanta, ba alamar wasa a amon muryarta tace "Me yasa take kiranka Abban Huda?" Dakewa yayi duk da fad'uwar da gabanshi yayi yace "Saboda ni da Junaid duk mun ce mata mun zama iyayenta, yarinyar kullum damuwarta ita ce mahaifi, amma yanzu kinga ta daina." Ba tare daya saketa ba ta juyo ta shafa kumatunshi tace "Je kayi wanka ka fito ka ci abinci." "To." Kawai yace ya shiga d'akinshi da tunanin k'ananan iskancin da Maryama ta taho mishi dashi kuma, shiryawa yayi ya fito ya sameta suka karya. Amar na saman hanya lieutenant ya kira shi kan yana so ya tura ma Ammar kud'i ya bashi lambar account d'inshi, dan a ganinshi daya tambayeshi kud'i to baya da su ne shiyasa, ba dan haka ba zai tambaya ba dan rabon da sisin kwabo ta shiga tsakaninsu dashi har ya manta, tun bai fara aikin likita ba ya tsaya da k'afafun, matsala ko wacce ta shafi karatunshi ce shi ke tsaya ma kanshi. Amar dai cewa yayi wallahi baisan komai a game da abinda ya shafi Ammar ba, shi kuma lieutenant yana jin ba zai iya tambayar Ammar d'in ba dan haka yace Amar ya bud'e mishi sabon count a bankinsu, yana zuwa aiki ba b'ata lokaci yayi komai ya ga sai sa hannun Ammar da yake buk'ata, hakanne yasa shi kiranshi dan ya fad'a mishi ya zo, amma mummunan labari sai police ya d'auki wayar ya fad'a mishi abinda ke faruwa, tun saman hanya Amar ke maimaita jikka sha biyar d'in me da Ammar zai yarda a d'aure shi akan ta, da wannan takaicin ya isa ofishin yayi bailinshi. Ana fitowa dashi ya ga Amar ne sai yaji ba dad'i, tsaye yayi yace "Dama wannan yaron ne ya zo fito dani? To babu inda zanje." Rai b'ace Amar yace "Ammar kar kayi taurin kai mana, ba wasa na zo yi ba." "To yi min fad'a ubana." Shiru Amar yayi yana kallonshi, ni yake kamar ya rufe shi da duka, amma yasan ko yayi haka shine zai sha wahala, a kausashe yace "Wuce muje." "Babu inda zanje, an fad'a maka ni bana da kud'in fitar da kaina ne? Abba nake si ya zo wajen nan, inba haka ba kuma ina nan wallahi." Juyawa yayi cike da takon isa da k'asaita ya shiga ciki aka rufe shi, harara Amar ya dalla mishi daga nan yace "Kai ka sani ka tabbata anan." Da kallon zaka gane kurenka ya bishi yace "Zamu had'u ne zaka san ka harare ni yaro." Da fari Amar shafawa yayi da al'amarin ya shiga harkokin gabanshi, saida ya tuna waye tagwaicinshi kad'ai ya sake kiran lambarshi, yanzu ma police ne suka d'auka, dan haka baiyi k'asa a gwiwa ba ya garzaya douanes ya samu lieutenant, yana fad'a mishi lieutenant ya rufe ido yana zabga masifa ta inda ya shiga bata nan yake fita ba, cewa yayi ya tafi kawai ya barshi can shiya sani amma shi babu inda zaije. Ummy ya kira a waya da niyyar yace ta lallab'i Abba, amma sai yaga tafi ma d'aukar zafi fiye da Abban, ita ma haka ya rabu da ita ya kira wayar Ammar aka bashi shi a waya, rarrashin duniya yayi dan ya fito amma Ammar sai yaga rayuwarshi ma bata da anfani, kenan babu wanda zai zo? Kashe wayar yayi ya bayar aka aje ya koma ya kishingid'a kamar a gadon sarauta yana ci gaba da tasbihi ga ubangiji yana kuma jiran yaji wa zai zo. Bayan magriba lieutenant ya dawo gida, a d'aki ne yake fad'a ma Zeituna cewa "Kinji wannan mahaukacin yaron abinda yayi?" Tasan sarai da wa yake dan haka bata kula shi ba ma dan bata ji dad'i ba, saida ya kalleta yace "Dake fa nake magana kina jina." Cikin d'an fad'a fad'a tace "To me kake so nace maka?" "Ban gane ba? Ina fad'a miki Ammar yana ofishin yan sanda kuma d'an uwanshi yaje yayi belinshi amma ya k'i tahowa wai sai naje da kaina, shine zaki fad'i haka." Cikin gatse tace "Oho ashe sunansa Ammar, ai na d'auka baya da suna ne." Kallonta yayi yace "... *Comment ya sani muku typing, ku ci gaba da haka zakuji bayani.* *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 🇳🇪 *TAURARIN NIGER* ```(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)``` ✪{T . N}✪📖🖊️ https://www.facebook.com/101305508365889/posts/101311008365339/?substory_index=0&app=fbl _Bismillahir rahamanir rahim_ _43_ "Ke wai ya kike neman b'ata min rai ne? Ya ina miki magana kuma kina magana kan wani abu daban." Ba alamar farin ciki ita ma tace "Na fad'a maka gaskiyar abinda ke raina shine, bana jin dad'in halin ko in kula da kake nuna mishi, shi ma fa haihuwarshi akayi, yana da rai da zuciya, yana jin zafi haka kuma yasan meye farin ciki, dubi ka gani d'azu kafin fitarka a gabana ka kira d'an uwan haihuwarshi kake tambayar lambar account d'in shi, me yasa shi baka kira shi ba? Kana jin kunya ne saboda shine babba ko kuma saboda baka k'aunarshi ne? Ni ban tab'a ganin iyaye irinku ba wallahi, gaskiya Abban Ammar ba zan yarda na haifi abinda ke cikin nan nawa ba shima kana nuna mishi wannan k'iyayyar, sam ba zan lamunta ba wallahi, gwara ka fad'a min tun yanzu in baka son 'ya'yanka ne saina zubar da cik..." "Ke." Wannan tsawar daya mata ce tasa tayi shiru tana kallonshi, baya k'aunarshi? Baya k'aunar 'ya'yanshi? K'iyayya? To wai duk meye na fad'in haka? Me na aikata da yasa ta tunzura haka har take fad'in maganganun nan? Kallonta yayi sai dai ya kasa cewa komai yana son sanin abinda take nufi, ganin bai ce komai ba sai kallonta yake yasa ta matso kusanshi ta rik'o hannunshi tana mai tausasa muryarta tace "Abban Ammar, kayi hak'uri da d'aga muryar da nayi a gabanka, amma ka sani wallahi abunne baya min dad'i ko kad'an, bansan ko har yanzu baku fahimta bane, ni marainiya ce babu uwa babu uba, nayi wayo a tare dasu amma ban girma dasu, sai dai duk da haka nasan soyayyarsu da yanda suka jani a jikinsu, hakan yasa har yanzu ina kewarsu kewar kulawarsu gare ni, duk sanda na tuna saina zubar da k'walla, haka duk sanda na ga maraya irina saina tausaya masa, karo na farko da naga wanda iyayensa ke raye kuma nake jin tausayinsa, shine Ammar, yana rayuwa tare daku a gida d'aya, amma hakan baisa kun iya fahimtarshi ba, a d'an zaman da nayi tare da ku da bai haura wata d'aya ba na lura da abubuwa da dama." Saida ta share hawayen da suka taho mata sannan ta ci gaba da cewa "Ban tab'a ganin Ummy ta amsa sallamarsa ba, ban tab'a ganin ta amsa gaisuwa ko maganar da zai mata cikin dad'in rai ba, hasalima yana shigowa inda take zaka ga ta canza fuska daga murmushi zuwa had'e rai, haka zai juya ya fita ba tare data bishi da kallo ba, bata damu ya ci abinci ko bai ci ba, ya ya kwana ya kuma ya tashi? Amma Amar, haba-haba take dashi da nuna masa kulawa, bayan ta amsa gaisuwarshi zata zata tambaye shi abinci fa? Idan yana buk'ata da kanta take bashi ya ci, to me yasa shi d'ayan bata mishi haka, ka duba kaga lokacin bikinsu, Amar na ta kai da kawowa tsakanin waje da d'akinta suna ta shawara, amma shi Ammar shi kad'ai yake harkokinshi babu mai kula shi a gidan nan, kowa d'ansa ya sani kowa ya kama wanda yake k'auna ya rumgume, to me yasa? Shi ba d'an gidan nan bane? Ko kuma wani abu ya muku wanda kuke hushi dashi har haka?" Kuka ne ya ci k'arfinta ta sunkuyar da kanta, saida ta saita nutsuwarta kafin ta d'ago tana kallonshi tace "Wallahi idan nice ake nuna wa wannan bambamcin na tabbata zan iya cutar da kaina, dan zanga kamar babu mai so na ne kawai gwara ma na mutu, Abban Ammar dan Allah ko sau d'aya ne ka zauna da yaronka ka fahimci matsalarshi kasan me yake ciki, ina tabbatar maka cikin sauk'i zaka fuskance shi, misali ni mana, wa zaiyi zaton zan samu wata girmamawa daga wajenshi? Amma sai gashi na ci darajar samun sunan uwa daga bakinshi, dan Allah kayi tunani akan abinda na fad'a maka, idan har kayi tunanin abinda ya dace nasan Ammar zai kwana gidan ubanshi yau, idan kuma kayi tunanin daka saba yi kullum to zai kwana a magark'ama, amma ka sani kar kuyi kuka da kowa duk ranar da kuka kaishi mak'ura har yayi abinda sunanku zai bazu a cikin gari." Sakin hannunshi tayi ta shiga ban d'aki, gaba d'aya lieutenant rasa jijiyoyinshi yayi kamar an tsinkasu, yana so ya gyara ko da tsayuwarsa amma ya gagara, sai dunk'ule hannunshi da yayi sosai kamar zai naushi wani, yafi minti ashirin a wurin nan kafin ya samu da k'yar ya d'aga k'afarshi ya juya ya fita, lambu yaje ya samu kujera ya zauna, durmiya yayi tunanin abinda ta fad'a mishi, babu komai a ciki face zallar tsagwaron gaskiya, to amma inda matsalar take shi bai tab'a tunanin hakan rashin kyautawa ne ba, bai tab'a tunanin hakan zai iya zama wani abu ba duba dashi ba yaron goye ne ba da sai an kula dashi, da wannan tunanin ya kasa katab'us sai tubka da warwara yake. Ko da ta fito bata ganshi ta fito da niyyar zuwa wajen Amna, acan ta hangeshi zaune cikin lambu yayi shiru, girgiza kai kawai tayi ta wuce inda zata je, saidai a tunaninta ba zai je ya dawo da shi ba, dan haka ta tafi da sake wani shirin da zaisa dole yaje. K'wank'wasa k'ofar tayi hakan yasa Amna tahowa da sauri, tana bud'a k'ofar ta ga Zeituna take ta bayyanar da damuwarta tare da fuszar da iska, kaucewa tayi a hanya ta shiga ciki sannan ta mayar da k'ofar ta rufe, juyowa Zeituna tayi ta kalleta tace "Amna lafiya kike?" Cike da damuwa tace "Aunty Zeituna ina lafiya, yah Ammar tun safe ya fita har yanzu bai dawo ba, ya fad'a min zai jima amma ban d'auka zai jima haka ba, wallahi gabana sai fad'uwa yake ina jin tsoron abinda ya same shi." Kallonta tayi da tausayawa tace "Kenan baki san mijinki na ofishin 'yan sanda ba?" Zaro ido tayi tsoro da tashin hankali ya ziyarce ta tace "Ofishin yan sanda? Meya faru dashi? Wane laifi yayi?" Dafata tayi tace "Kwantar da hankali Amna, ba wani babban laifi bane." "Amma kuma yake hannun yan sanda? Me yake faruwa aunty Zeituna?" Nan ta kwashe komai ta fad'a mata, cikin kuka wanda yafi kama dana shagwab'a tace "Yanzu aunty Zeituna Abba ba zai je ba kenan? A can zasu barshi ya kwana? Allah ba zai yiwu ba." Murmushi ta mata tace "Nima na zo fad'a miki abinda in ki kayi ne mijinki zai kwana tare dake yau." Da sauri ta rik'e hannunta tace "Fad'a min aunty Zeituna, me zanyi?" Cikin murmushi tace "Kawo kunnenki kiji." Wani abu ta fad'a mata wanda nima an fad'a min abinda ta fad'a mata amma ni zan fad'a muku a rubuce, kallonta tayi tace "Kin tabbatar zaiyi aiki?" Cike da son tabbatar mata tace "Amna dole zai fito miki da mijinki ko baya so, kawai ke dai ki jajirce ki zama mai naci kan hallayar mijinki." Duk da tana jin ciwo a k'afafunta na bak'ar wahalar da tasha amma saboda k'arfin hali da gudu ta nufi d'aki tana fad'in "Nagode aunty Zeituna." Jim kad'an ta fito da mayafi ta yafa a kafad'a ta shiga madafa, kwandon saka kwanukan abinci ta dauko ta fito, kan teburin cin abinci ta nufa ta jera kwanonin abincin tare da robar ruwa da lemu da kuma lemu orange da ayaba, saida ta zo gaban Zeituna dake ta binta da kallo tace "Aunty haka yayi?" "Sosai ma, ai kawai ki basu mamaki." Ta fad'a tana kanne mata ido, tare suka fita inda Zeituna ta koma b'angarensu ita kuma ta fita, saida ta kai bakin titi kad'ai ta samu adaidaita sahu ta shiga, ba jimawa sosai mai adaidaitar ya sadata da inda zataje dan babu nisa sosai, bayan ta shiga ta fad'i wanda ta zo gani da cewa abinci ta kawo masa, abunka ga idan mutum wani babbu ne ko mai alak'a da babba, izinin ganinshi aka mata ta zauna inda aka nuna mata gabanta na ta fad'uwa dan bata tab'a zuwa ba sai yau dalilin mijinta. Da wani tako ne ya fito wanda yafi kama da fitowar sarki daga cikin gida zuwa kan karagar mulkinshi, kallonshi take a hankali soyayyarshi tana narkewa a zuciyarta, k'arfin halinshi da sababinshi yasa ta sakin murmushi, sab'anin shi da yana ganinta ranshi ya b'ace ya k'ara sauri a tafiyarshi ya k'araso wajenta, yana zuwa ba tare daya zauna ba ya zaro mata ido yace "Ke kuma meya kawo ki nan?" Saida ta daure sosai kafin ta samu k'warin gwiwar cewa "Wajenka na zo mana." Fizgo hannunta yayi ya mik'ar da ita tsaye yana fad'in "Amna baki da hankali ne? D'an iska kika mayar dani ko me? A wannan lokacin kika fito daga gida kika zo nan kuma da wannan shigar?" Kallon kanta tayi, riga da siket d'in na leshe wanda suka amshi jikinta sune matsalar? Ko kuma d'aurin data b'ata lokaci ta kashe wajen d'aura shi? Kwalliyar fuskarta ko kuma mayafin data yafa? Kallonshi tayi tana turo baki gaba duk tayi kalar wallahi kuka zan ma ka tab'ani, a hassale yace "Billahil azim kifar dake zanyi wurin nan kika min kuka, ke ni d'an iska ne?" Girgiza kai tayi da sauri tana fad'in "A'a." Rik'e k'ugu yayi yace "To uban wa yace ki fito haka? Kuma waya kawo ki nan?" Saida ta k'ara yin kalar tausayi sannan tace "Aunty Zeituna ce." "To waya kawo ki?" Ya sake jifarta da tambayar, saida ta d'anyi baya kad'an tana kallonshi sannan tace "Adaidaita...Ahhhhh." Ta fad'a da k'arfi saboda d'aga hannu da yayi kamar zai kifeta da mari, a hankali ta bud'e idonta jin bai sauke mata yatsunshi ba a kumci, kallonshi tayi sai taga ya k'ura mata ido yana kallo, da kankana ce da yanzu ta zuba a guje, amma ita saita tsaya ko kasheta zaiyi, abun ne ya bashi dariya sai kawai ya figo hannunta ta fad'a jikinshi ya rumgumeta yana dariya yace "Mahaukaciya, ke baki iya guduwa ba idan za'a dake ki." Cikin shagwab'a tace "To yah Ammar taya zan iya tsere maka? Mai guduwarma (Hamna) naga in kayi niyya kana ritsata duk inda take." Lumshe ido yayi yana sakin murmushi kafin ya d'agota yace "Yanzu to ki koma gida, amma k'asa zaki tafi in ba kya son ki jazawa masu adaidaita bala'i, kinji ko." Ya fad'a ba alamar wasa a tare dashi. Shagwab'e fuska tayi tace "To ai ni ban zo dan na koma ba, nan zan kwana tare da kai." K'ura mata ido yayi yana kallo, ya jima yana tausar kansa kafin yayi nasarar kwantar da hankalinshi yace "Amna kuka kike so kiyi ne?" Da sauri ta rik'e hannayenshi tana fad'in "Bana so, amma kuma ina nan tare da kai yah Ammar." "Me yasa?" Ya fad'a yana son k'watar hannayenshi, saida ta langab'e kai tace "Aunty Zeituna tace idan na zo nan dole Abba ma zai zo yayi belinka da kanshi." Kallonta yayi sosai yayi murmushi yace "Uwa ta shiga al'amarin?" Kai ta jinjina masa alamar eh, sai kawai ya zauna kan bencin ya sashi tsakiya yace "Zuba min abinci na ci kinji yarinya, tunda uwata ta shiga lamarin nasan ma dole zai zo." Murmushi tayi ta fito da kwanukan ta soma zuba mishi abincin, har ta d'auki cokali zata fara bashi saiya girgiza mata kai, aje cokalin tayi ta wanke hannunta ta fara bashi da hannunta, yana ci yake ce mata wai tayi hak'uri na rashin zamanshi gida a tare da ita, uffan ba tace ba sai yanka mishi loma da take tana aika masa. Tana komawa b'angaresu ta samu lieutenant a inda ta barshi, shiga tayi ta tsaya gabanshi tana kallonshi, ta jima tsaye amma bai motsa ba alamun baisan da zuwanta ba, ajiyar zuciya ya sauke tare da d'an juyo da kanshi hakane yasa ya ganta, cikin basarwa ya d'an had'e fuska yace "Ya dai?" Murmushi ta masa tace "Ba komai." Bai ce komai ba sai juyar da kansa da yayi, ita ma ba yanayin wasa a tare da ita tace "Yallab'ai akwai matsala fa." Kallonta yayi yace "Matsalar me kuma?" Saida ta gyara tsayuwa ta mayar da hannayenta bayanta sannan tace "Yanzu daga b'angaren Amna nake, na sameta tana ta kuka saboda rashin sanin halin da mijinta ke ciki, dana fad'a mata tayi hak'uri dan ba zaka je ka fito dashi saita d'auki mayafinta ta fita, da k'yar ma ta fad'a min tace zata je wajen mijinta ne tunda babu mai k'aunarshi." Kamar an tsikare shi haka ya tashi tsaye yana mata wani mugun kallo cikin d'aga murya yace "Babu mai k'aunarshi? Wai wace irin magana ce kikeyi haka? Taya kike tunanin zamu haifi d'an a cikinmu amma mu ce ba ma k'aunarshi, akan me zaki fad'a mata haka kuma har ki bari ta fita a wannan lokacin, ke a ina kika tab'a ganin haka?" Ba tare data nuna tsoron yanayinshi ba tace "Akan ku mana, kanku na fara gani." Jinjina kai yayi yace "Ok, to ni kuma yau zan nuna miki k'arya kike, ina son d'ana kuma ina k'aunarshi fiye da komai dana mallaka a duniya." Fuuu ya rab'ata zai wuce cike da shak'iyanci sai cewa tayi "Taya zan tabbatar ina daga nan bansan me ya faru a can ba?" Tsayawa yayi ya juyoya kalleta da mamaki, raina shi ne tayi kome? Shi kananta ne da zata mayar dashi abokin wasanta? Saida ya jinkina mata kai yace "K'arfin shaukin da zan nuna masa zai riskeki har gidan nan." Juyawa yayi ya fita ta bishi da murmushi Allah ya bada sa'a, tun a hanya yake k'ulla kalar k'aunar da zai nuna masa, to wai a kan me zata fad'a masa baya k'aunar d'an shi, ko bata san shine sanyin idaniyarshi na farko bane? Bata san duk suna mishi abinda suke mishi ne ba dan suna son ya gyaru ya zama na k'warai? Ta manta da duk fafutukar da yake saboda 'ya'yanshi yake yinta sannan Ammar shine magajinshi na farko? Me yasa bata tambaye shi me yaji ba a sanda aka fad'a mishi an rufe mishi? Amma ba komai zai nuna mata ba haka bane abinda take cewa ta ganin, da wannan tunanin ya isa ya baka tsandareriyar motar data sanar da jami'an babban mutum ya shigo, sanin sosai suka masa ba sanin shanu ba, dan haka suka sara masa cikin girmamawa ya shiga ciki, ikon Allah sai kallo, ganinshi hankali kwance matarshi na ciyar dashi cikin nishad'i, abinda ya aikata ya cancanta ya bibbige shi amma ba hali, k'wafa kawai yayi ya shiga inda zai samu belinshi. Cikin mutuntawa aka fad'a mishi ai Amar ya biya tarar kawai zasu iya tafiya, amma gobe da safe saiya dawo a musu sulhu saboda gaba, duk da haka saida ta d'ebo kud'in da baisan ko nawa bane ya zube kan teburin kafin suka fito, sai lokacin ne suka ga lieutenant, hannu ya d'aga masa yace "Abbana barka da dare, har ka iso?" Tasowa yayi daga bencin kamar k'aramin yaro sai kawai ya rumgume shi yana wani k'amk'ame shi da kwantawa kan k'irjinshi yana fad'in "Nasan kana min son da baka ma kowa Abba, dama nasan zaka zo, ba zaka iya bacci a gidan can ba idan bana gidan nan, ko ba haka ba?" Abun yafi k'arfin tunanin lieutenant, sai kawai ya tsinci kansa ya rumgume shi shima har da shafa kansa yana murmushin da baisan ko na miye ba yace "Gaskiya ne, ai indai har zaka kwana a nan to sai dai in gaba d'aya ahalin Gaga ne suka tare a wurin nan." D'ago kai yayi ya kalleshi ba tare daya d'aga daga k'irjinshi ba, turo baki yayi gaba irin tunda na samu ka biye min to bari na yi abinda na jima ina kewarshi daga gareku, sai k'ara narkewa yake jikinshi kamar zai shige cikinshi, Amna dake kallon ikon Allah tashi tayi ta wanke hannunta ta had'a kayan, kallonta lieutenant yayi yace "Shikenan 'yata sai ki taho wurin mijinki baki sanar da kowa ba." Murmushi kawai tayi kafin lieutenant ya d'agoshi daga jikinshi yace "To mu tafi ko?" Kafad'a ya d'aga alamar a'a kamar yaron goye, kallon zan ci ubanka a wurin nan lieutenant ya mishi tare da cewa "Meye kuma?" Cike da shagwab'a yace "Sai kace muje shalele." Anya yaron nan banda aljanu kuwa? Tambayar da lieutenant ya ma kanshi kenan, wato dan ya ga ya zo shine saiya mishi iskanci yasa ranshi ya b'ace har ya kasa yin abinda ya fad'a, daga Ammar d'in har Amna kallonshi suke suna jiran suji me zaice, rarraba ido yake ganin jami'in dake tare dasu ne kawai yasa yayi murmushi yace "To muje shalele." Dariya yayi ya rik'e hannun lieutenant da kuma hannun Amna suka rankaya yana fad'in "Daga yanzu ni ma na zama shalelenka, kaga Amar shalelen Hajia ne ni kuma na ka ko Abba?" "Umm." Kawai ya fad'a ba tare da yace komai ba, kallonshi lieutenant yayi yace "Motarka fa?" Saida ya bud'a ta lieutenant ya shiga ya hakimce sannan yace "Tare da Abbana zan tafi, gobe na dawo na d'auka daga nan nima saina shigar da k'arar wannan banzan." Shiga sukayi duka Amna na baya yace "K'arar me kuma?" Saida ya kalleshi yace "Abba k'azafi ya min wai ina saka kayan soja, har da cewa wai ina da bindiga." Kallonshi lieutenant yayi irin kallon nan na anya Ammar ba gaskiya bane kuwa, saida ya tayar da motar suka d'auki hanya kafin yace "Ka daina shiga rigima Ammar, bana jin dad'in haka fa, wai kai baka san ka girma bane?" "Zan daina Abba, dana gama da wannan yaron shikenan." Ya fad'a yana kallon titi, *meye nufinshi akan Jano ne? Ni dai nasan da abinda yake so dashi*, suna zuwa gida suka fito a mota suka nufi hanyar da zata sadasu da b'angarensu, dole ta inda lieutenant ya paka mota indai zasu wuce sai sun bi ta k'ofar shiga falon Hajia, hakanne yasa Ammar hangota zaune kan kujerar mulki, murmushi yayi ya tunkari shiga ciki, rik'oshi lieutenant yayi yace "Ina zaka kuma? Wuce ka bi matarka." Langab'e kai yayi yace "Abba Hajia zai gaida duk yau bamu had'u ba duk bana jin dad'i." Wani kallo ya masa yace "Ammar uwata ce fa, karka ja min zagi yanzu a daren nan mana." "Allah Abba ba zan sa ba, nayi alk'awari." Yana fad'a ya shiga ciki da sallama, Amna kam da take jin haushin tura mata yer uwarta wani wuri bata shiga ba sai na su b'angaren data nufa. Yana zuwa kamar an tura shi ya durfafeta ya rumgume tare da sumbatar goshinta yana fad'in "Hajiata ikon Allah, wallahi duk nayi kewarki wunin nan kawai da ban ganki ba." Tareshi tayi daga jikinta tana goge goshinta da fad'in "Kai rabu dani dallah, wai kai baka da lafiya ne?" Kallonta yayi ya dafa saitin zuciyarshi yace " Yanzu ne kawai na fara jin na samu lafiya da nayi tozali dake." Da k'arfi ya sake fizgo fuskarta ya sumbaceta a kumatu yana fad'in "Ina sonki, saida safe, karki bari kishina ya hanaki bacci." Saida ta marmad'a ido saboda yanda ya fincikota, da kallo ta bishi tana mamakin halin wannan k'waya d'aya tak dake saka mata hawan jini, yanda ta kafe k'ofar da ido har ya b'ace ma ganinta sai kawai taji tana murmushi, kamar an tsikareta sai kuma taja tsaki tana fad'in "Mahaukaci." *Capital* Baccin marar dad'i har ya fara d'aukarta d'aya daga cikin ma'aikatan gidan ta shigo ta kirata, fitowa tayi jiki a sanyaye ta zo ta tsaya gabanta kamar yanda ita ma take tsaye, kasa d'aga kai tayi ta kalleta saboda tun tana tahowa taga kayan bacci ne jikinta masu shegen kyau da d'aukar ido, kamar saukar aradu ta kashe ta da mari tare da mata tsawa tace "Idiot, ina tsaye shine ke ma zaki tsaya min a kai haka." Dafe kumci tayi ta bud'e baki ta kalleta tace "Kika mare ni?" D'aga hannu ta sakeyi zata sake marinta tayi baya da k'arfi tana fad'in "A'a wallahi, ko uwata ban rayu da ita ba ta yanda zan iya fad'a miki ranar data d'aga hannunta a kaina, dan haka ya tsaya nan gaskiya." Cike da iko tace "Ni kike fad'awa haka? To bari kiga abinda zanyi, ubanki zan fad'a ma ya sanar dake k'arfin ikona, idan ya fad'a miki da kanshi zaki fi ji da kyau." Juyawa ta shiga ta wata k'ofa da zata sadata da d'akin baccinshi, tab'e baki Hamna tayi ta juya ta koma ni'imtaccen d'akinta ta kwanta, amma abun takaici sai ga mahaifinta cikin jallabiya tare da matarshi sai wani rirrik'eshi take tana kukan munafurci, bata san me ta fad'a mishi ba? Bata san meya faru ba kawai saiya rufe ta da fad'a kamar saukar ruwan sama, saida ya gama sannan ya jaddada mata duk abinda Aissata ta sakata tayi ko bata so dan ita ce mai gidan nan, sannan idan ta mata musu Allah ya isa bai yafe mata ba, juyawa yayi suka fita sai kawai ta fashe da kuka, duk rashin kirkin Hajia suna sakata su wala, babu takura babu matsi sai in ka taka mata doka, amma nan, lallai ma. To fa hakan data faru ne yasa washe gari da safe ta kirata, tana zuwa tace "D'aki na zaki gyara min ki min shinfid'a, idan kin gama ki wanke ban d'aki da kyau sannan kiyi turare, idan kin gama sai ki zo na fad'a miki aiki na gaba da zaki min." Hararanta ta farayi sama da k'asa kafin daga bisani ta tuna kalmar Allah ya isa da mahaifinta ya fad'a mata, cikin ladabi tace "To." Ta juya ta shiga d'akin, duk ni'imar duniya ta taru a d'akin nan, kud'i ko nace kayan kud'i kamar zasuyi magana da baki tsabar yanda aka tarwatsa su, komai na kud'i ne d'aruruwa ko milyoyi, gyarawa tayi ta share ta wanke har ban d'akin ta goge komai sannan tayi turare, kama daga na ruwa na tsintsiya har na wuta, hakan yasa d'akin k'ara sanyaya da sanyin k'amshi, tana idarwa ta fito ta fad'a mata, ki shiga madafa ki samu *Betrice* ta baki jadawalin duk abinda nake ci da kuma lokacin da nake cin shi, daga yanzu ke ce mai wannan alhakin." Yawu ta had'e ba tace komai ba kawai ta wuce madafar, tana zuwa ta fara fad'a mata "07:30 zaki kai mata lipton a d'akinta, 08:00 zaki kai mata ruwa da matsatsun kayan itatuwa a d'akin motsa jiki, k'arfe 09:00 daidai zaki shirya mata petit déjeuner (karin kumallo) a kan table, da k'arfe..." Hannu ta d'aga mata tana yatsina fuska tace "Dakata dan Allah, ki samu takarda ki rubata min zan duba daga baya, bana da lokacin wannan shashancin." Yana fad'a ta barta nan tsaye tana kallonta, kamar yanda ta buk'ata haka ta ruba ta mata komai ta kai mata, daga wannan lokacin ta fara aiki dan matar muguwar yar tamne-tamne ce bata gajiya da had'id'iya, bata awa d'aya bata buk'aci wani abu ba, ko ba komai taji dad'i daya zama ita ce a gidan ba Amna ba, dan da ita ce to tana iya yin zuciya ta bar gidan sai kawai an ganta ta koma Maradi, sai dai Allah ya isar ta bita kam amma ba zata d'auka ba, da wannan yau ta kwanta baccin gajiya saboda bata huta ba ko kad'an sai kai da kawowa, abunka ga gidan gwamnati ga girma daga wani wurin zuwa wani tafiya ce mai tsayi. *Gaga's house* *Ko da* aka wayi gari Jibril ya kaiwa Hajia santalelen rak'umi a matsayin yaba kyautar samun Jamila a budurwa, har ya mik'e zai fita boss ya shigo tare da Amna dan ta gaishe da iyayensu, Hajia na ganinshi ta dafe fuskarta da nufin kar ya mata sumbatar nan, yana ganin haka ya zo kusanta ya ruk'umk'umeta ya sumbaci bayan hannunta dan ta rufe fuskarta da hannuwan, yana sakinta ta kalleshi tace "Jarababbe, wai kai ba zaka iya rayuwa ba tare daka shiga harkata bane?" Daf da ita ya zauna yace "Ko kad'an ai, idan kinga haka sai in babu ke ne a duniya." Hararenshi tayi tace "Fatan mutuwa kake min?" Kallonta yayi yace "Kar dai kice min ba kya son mutuwa ke ma?" Wata hararar ta sake mishi tace "Uwarka ce zata mutu ba ni ba." Murmushin rainin hankali ya mata yace "Toda uwata ta mutu me zai hana a d'auke Alhajinki? Tunda naga shine tsoho a gidan nan." Wani uban dundu ta sakar masa a baya tace "Ammar bana son iskanci, ina son shi har yanzu bana so ya barni." Murmushi kawai yayi ya kalli Jibril yace "Halan kai ka siyo waccen rak'umin?" Gira kawai ya d'aga mishi alamar eh, kallon Amna yayi ya mik'a mata hannunshi yace "Zo ki gaishe ta mana." Matsowa tayi ta d'an sunkuya tace "Ina kwana Hajia." Ba annuri a fuska tace "Lafiya lau." Mik'ewa yayi yace "Kewace irin gaisuwa ce haka? Dallah malama haka zaki mata, rumgumeta zakiyi, ina so kema ki zama mafi soyuwa a zuciyarta kamar yanda tafi so na sama da kowa." Da k'arfi ya jawo Amna ya tallabo Hajia ya mannesu wuri d'aya yace "To rumgumeta ki sumbaci kumatunta." 😂 *Covid19 inji aunty* Amna dake jin abun wani iri kasawa tayi, Hajia kuma sai k'ok'arin tureta take kamar kashi tana fad'in "Kai kana da hankali kuwa?" Bata ankara a sunkuyawar nan da tayi sai kuwa ya sauke mata k'ulli a baya yana fad'in "Ke dan ubanki rumgumeta." Bata shirya ba sai kuwa ta fad'a kan Hajia da k'arfi tana sakin tarin da bata shirya zuwanshi ba, da sauri ta rumgumeta ta raba jikinta da nata tana dafe bayanta tana kallonshi, yanda duk ta shagwab'e fuska kuma saita kashe shi a wurin, take ya jawota ya rumgume kuma yana shafa mata bayan yace "Yi hak'uri kinji chouchouta (shoushouta), kin yafe min ko." D'aga kai Amna tayi ta raba jikinta da nashi saboda fitowar iyayensu, kafin su gaisa kuma Marya suka shigo ita da Junaid. *Alhamdulillah* *Yawan sharhi yawan rubutu.* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 _44_ Ko da ta gaishe da kowa ya amsa da sakin fuska amma banda Zeinabu da Hajia, Amar ne suka shigo shima tare da Umaimah, gaisawa akayi sosai inda Hajia ta zaunar dashi kusa da ita tana ta mishi tambayoyi kamar yaro, shi kuma duk a takure yake jin kanshi a kusa da ita, kallon Umaimah tayi tace "Zo." Kusanta taje ta zauna kanta k'asa, saida ta kalleta ta nuna shi da yatsa tace "Kinga wannan? Shine farin ciki na, kiyi iya k'ok'arinki wajen faranta masa rai, ni kuma na miki alk'awarin duk abinda kika nema a wajena zaki samu, kinji ko?" Kai kawai ta d'an d'aga alamar to, Alhaji ne ya shigo da sallama da farin ciki a fuskarshi na ganin ahalinshi, nan ma wata gaisuwar ce ta b'arke tsakaninsu kafin ya kalli kowa yace "Masha Allah, tunda kusan duk mun taru muje mu ci abinci tare mana." Duk da akwai wanda basu buk'atar cin abinci amma basu mishi musu ba sun nufi kan babban teburin, Amar da Hajia ke rik'e da hannunshi yana son ya sub'uce amma ta rik'e, ta bayanshi Ammar ya mazge mishi k'eya yana fad'in "Jiya kaine ka hareri ni ko?" Dafe kai yayi yana kallonshi, a hassale Hajia tace "Ammar meye haka? Zan ci uwarka fa." Ganin ko kulata baiyi ba yasa tace "Yaje ya hararekan to mugu mak'etaci." Duk uwayen kowa ya samu ya zauna sai kuma matasan maza, su Amna kuma su suka zuzzuba abinci, ana fara cin abinci Ammar ya kalli Amna ya mik'e tsaye da farantinshi a hannu ya zagaya har inda take, kama hannunta yayi suka nufi hanyar d'akin Ummy yana fad'in "Aljannata zo muje d'akin Ummy na ciyar dake." Rufe baki Amar da Jibril sukayi suna dariya, sai Junaid daya bishi da kallo yace "Bak'auye anyi agogo." Saida ya wani sassako wandonshi yayi k'asa kamar yanda gayun nan keyi kafin su waye yace "Dole mana, mata wasa ce, ita ce mahutata dole na kula da ita." Jibril zaiyi magana yana dariya Ummy ta kalleshi tace "Dan Allah ku rabu dashi, kada kusa muji abinda kanmu ba zai iya d'auka ba." Ba tare daya daina tafiyar shak'iyancin nan ba har suka shiga d'akin Ummy su dai suna binsu da kallo, suna kammala cin abincin suka fito, kusa da Amar ya tsaya yace "Yaro tashi muje ka sauke ni, banda mota a hannu." Kallonshi Ummy tayi kamar tayi magana sai kuma tayi shiru, Hajia ce tace "Halan ka siyar da motar?" Kallonta yayi yace "To Hajia idan rashin kud'in ne zaisa na siyar da uwar gidata ai ina ga kina da kadarori ajiye, ko sark'ok'in da kike sakawa ma kad'ai sun isheni rayuwa idan na siyar." Wani kallon sai dai haushi ta masa tace "Dad'inta dai gadar arzik'in nayi tun daga gida, a sanda mahaifina yayi zamaninsa babu wanda bai san shi ba." Murmushin gefen labb'a ya mata yace "Yanzu? Ai har yanzu mu yana zamaninshi a wurinmu, tunda Alhaji ya fad'a mana duk shine silar arzik'in nan da muke ciki, da taimakon Allah da taimakonshi da yyanzu watak'ila muna can anata fama." Wani murmushin jin dad'i tayi ance arzik'i daga mahaifinta ya fito tayi, yana kallonta saiya bushe da dariya yana fad'in "Kinsan wani abu Hajiata, Allah sai naga k'aramin bakinki nan na ki zaiyi mugun kyau idan kina yanko lomar tuwon dawa kina shinfid'ata kan miyar daddawa kina jefawa baki." Wata irin tattausar dariya Alhaji yayi yana kallonta yace "Ai kuwa saima ka gani da idonka, abun sha'awa ne sosai, gata kuma gwanar iya tuk'a tuwo yayi taushi laushi da santsi." Wannan karan kusan babu wanda baiyi dariyar ba sai Hajia da ranta ya b'ace ta kalli Alhaji, sama da k'asa ta harare shi sannan ta ci gaba da cin abinci ta, Ammar dake dariya har da rik'e ciki ne ya kalli Amar yace "Kai nake jira." Lieutenant ne ya d'auki makullin motarshi ya jefo mishi yana fad'in "Je da wannan." Cab'ewa yayi yace "Abba kai fa?" Kallon Amar yayi yace "Shi saiya kaini." Bai ce komai ba ya zagaya wajen da Hajia ke zaune ba tare data kula ba taji ya sumbaceta a kumci yana fad'in "Uwar gidana saina dawo." Kusan Husseina yaje ita ma ta samu nata rabon tare da cewa " 'Yar tsakiya kenan mai ban haushi." Saida yaje har inda take tsaye ita ma ya sumbaci kumcinta yace "Wannan ce amaryata." Kusan lieutenant ya tsaya ya sunkuya ya mik'o mishi kumatunshi alamar ya sulbace shi, saida ya kalli Ummy da Hajia da sauran mutanen wurin wanda suma duk idonsu akansu suke, yana kallon Zeituna ya fahimci ma'anar kallonta sai kawai ya danna mishi wata k'aramar sumba a kumci, mik'ewa yayi daga sunkuyawar yace "Abba baka ce komai ba." Kallonshi yayi to shi me zai ce? Saiya tuna da jiya sai kawai yace "A dawo lafiya." Murmushi yayi sosai yace "Nagode Abba na, kai bai ma ka dawo lafiya." Zeituna ya kalla yace "Uwata saina dawo." Da murmushi a fuskarta tace "A dawo lafiya, Allah ya bada abinda aka je nema." Murmushi ya mata yace "Nagode." Ummy ya kalla, ido cikin ido, kallo mai ma'anoni da dama mai wuyar fassara, ba tare daya daina kallonta ba ya wuce yana dank'ara gilashinshi a fuska wanda ya fito mishi da manyan fararen idonshi. Haka kawai ta samu kanta cikin yanayin rashin jin dad'i, ta kasa d'auke ido daga gare shi har ya fita, kowa ya ma magana banda ita, har gaisawa da akayi tun a falo bakinshi bai had'u da nata ba, tana kallo sai wata ya kira da sunan uwa ba ita ba, sai taji kamar tayi ihu ko wani ya tambayeta lafiya har ta fad'a mishi abinda ke ranta, a hankali ta dawo da kallonta kan farantin abincinta, amma sai taji ya fita a ranta sai kawai ta mik'e zata bar wajen, idonta ne suka sauka kan Zeituna da ita ma a lokacin ta kalleta ganin ta tashi, had'e mata fuska tayi tare da jan dogon tsaki wanda bata san ma ya fito fili ba ta bar wajen. Da kallo kawai aka bita inda lieutenant ke tunanin larurar ciki ce kawai, Hajia kuma take ganin kishi ne ba komai ba, haka suka gama cin abincin sai dai babu wani nishad'i tunda Ammar ya tafi bare ayi raha, haka kowa ya tashi ya kama gabanshi sai kuma randa ta juyo aka sake irin wannan zaman, dan abune mai wuya ka gansu zaune hakanen wuri d'aya dukansu. Ko da yaje ya samu Jano a can, insp. ya basu hak'uri yace su ba juna hak'uri kuma a kiyaye gaba, rumi-rumi suka fito daga ciki kowa ya shiga motarshi, saida Ammar ya kira wani matashin saurayi dan ya zo ya bi bayanshi da motarshi saiya kaiwa lieutenant tashi a can ofishin shi, Jano na daidaita motarshi zai fita ya fito daga tashi motar ya same shi, saida yasa ya sauke gilashin suka kalli juna yace "Jano karka manta, a dalilinka na tab'a shiga prison, dan haka kaima ka shirya shigarshi ko da na kwana d'aya ne, ka dai san nasan shige da ficenka da kuma sana'ar da tafi shigo maka da kud'i." Saida ya nuna mishi yatsa yana kalkad'a shi yace "Ka kula." Wucewa yayi ya barshi nan, tare da yaron da ya zo suka tafi shi a motar lieutenant har suka isa. Yayi mamaki sosai da aka ce wai Ammar na son ganinshi, Ammar dai daya sani? A gaskiya ba dan Ammar d'aya ya sani ba a duniya idan ka cire *sahabi Ammar bin Yaseer wanda suka fara shahada a musulunci* da sai yace shine amma ba nashi ba, dan nashi in ya zo kai tsaye yake shiga ko da yana tare da bak'i ne, izinin shigowa yasa aka masa, saida ya ganshi ya dai tabbatar shi d'in ne, cikin nutsuwa ya zauna kan kujerar dake fuskantarshi ya bashi makullan yace "Abba gashi, nagode." Shima cikin yanayin kulawa yace "Har ka dawo ne? To ya ake ciki?" "Ba komai Abba." Ya fad'a babu walwala tare dashi, saida ya gyara zama ya kalli lieutenant yace "Abba, akwai wata masaniya da nake son baku kan wani mutum, bansan ko kana so ba?" Kallonshi yayi da murmushi, ko ma wanene tashi ta k'are cewar lieutenant, amma sai yace "Zamu so mana idan ya shafi aikinmu." Sai kuma kawai ya mik'e zai fita yace "Shikenan, zan nemo." K'ofa ya tunkara lieutenant ya bishi da kallo, me yake nufi kuma? Ganin zai fita yasa yace "Ammar." Juyowa yayi da fad'in "Na'am." Saida ya kalli agogo yace "Da k'arfe hud'u na yamma ka same ni gidan gona ta dake kusa da *Olga oil*." Da d'an murmusawa yace "To Abba." Fita yayi da wayarshi a hannu yana neman wata lamba, saida ya shiga mota ya zauna sannan ya aika kiran, bayan an d'auka sun gaisa ya fara mishi wasu tambayoyi, sun d'an jima suna magana kafin daga bisani yace "Ka tabbatar motar kayanshi ce ake d'orawa?" Daga d'aya b'angaren aka ce "Na tabbata yallab'ai." "Ya yanayin lodin yake?" Ya tambaya, daga can tace mishi "Eh to, kwalayan (karton) indomie ne da lipton, sai atampopi daga sama da shadda, sai kuma buhunan shinkafa a sama." Wani murmushin da shi kad'ai yasan ma'anarshi yayi yace"Nagode, zan sake kiranka." Yana kashewa ya tayar da motar ya d'auki hanyar, wannan binciken k'wak'wafin shi ya wuni yana yi, daga nan zuwa can daga can zuwa nan, waya kuma har ya gaji da amsawa duk saboda son kawo k'arshenshi, sai misalin *12:30* ya d'auki hanyar komawa gida cike da gajiya, kai tsaye b'angarenshi ya nufa da makulli a hannu da waya, da wata zazzak'ar sallama ya shiga sai dai babu kowa bare bare a amsa mishi, falon yasha gyara sai k'amshin turaren wuta yake na jonawaa lantarki, ga kwanukan abinci da aka jera wurin ya k'ayatu, murmushi kawai yayi ya aje makullin da waya akan teburin tsakiyar falon ya shiga d'akinta. Tana tsaye gaban madubi tana d'aure k'ananan kitsonta, yana ganinta ya fad'ad'a murmushinshi da fad'in "Wow, duniyata." Da sauri ta juyo ta kalleshi, murmushi tayi ita ma tare da takowa cike da kunyar kayan data saka, tana zuwa ta narke a jikinshi tana sauke numfashi a hankali, ni'imtaccen k'amshinshi turarenshi ne ke ratsa hancinta, shafata yake tare da mamatsa bayanta yana cika hannu da tsokar bayanta ido rufe, har tsakiyar kanshi yake jin duk wasu albarkatun jikinta na sake samun matsuguni a na shi jikin, turaren na kwantar mishi da hankali sosai, a hankali ta d'ago kai ta kalleshi, kallon tattausan fuskarsa wacce ke canza launi duk sanda ta so yasa ta lumshe ido, saida ta d'aga k'afafunta ta kai bakinta daidai na shi ta sumbata, babu wata k'ara ko sauti, saidai tasirin sumbar yasa ya lumshe ido, lokaci d'aya suka bud'e ido a tare suka kalli juna, murmushi ta sakar masa tace "Ka gaji ko yah Ammar?" Girgiza kai yayi cikin sanyin murya yace "A'a ba yah Ammar ba, ki saka min wani sunan na daban." Saida ta jujjuya matsakaitan idonta tace "Umm! Kamar wane kenan kake so?" Murmushi ya mata yace "A ganinki wane sunan na cancanta? Ni dai kinga na baki sunan duniyata, saboda kin zama dunuyata, ni kuma fa me na zama naki?" Saida ta k'ara rik'e k'ugunshi da kyau da hannayenta tana kallon k'asumbarshi sannan tace "Nima ka zama duniyata, sabuwar rayuwata kuma farin cikina." Raba jikinshi yayi da na ta ya d'an turata gefe ya k'ura mata ido, kallonta yake kamar zai had'iyeta, dogon wandon jeans bleue dark da riga bleue light mai hannaye iya damtse, dogayen takalmi bak'ak'e sai yar gajerar kwalliya da tayi, juyawa yayi yana zagayata dan ganinta da kyau, masha Allah duk da tana da gaba sosai, amma kuma sama suke can mak'ale da k'irji, bayan nan kam tubarkallah yau data saka wando ya zauna mata daram akansu sai abun ya bayar da citta. Kiran sallah a masallacin dake jikin gidan nan ne yasa yace "Bari na dawo daga masallaci, ina nan tare dake sai la'asar zan fita." Ban d'akinta ya fad'a yayi alwala ya fito, gabanta ya tsaya ya danna mata wata mahaukaciyar sumba a goshi sannan yace"Saina dawo." Tare suka fito daga d'akin shi ya fita ita kuma ta zauna zaman jiranshi. Tunda Ummy ta shiga d'aki bata sake fitowa ba, har asibiti ake ta kiranta wasu k'ananan ma'aikatan na tambayarta kan wani abu idan ya shige musu duhu, har akayi sallah azahar aka gama bata fito ba, damuwa da halin da take ciki yasa Zeituna shiga d'akinta dan ta gani, da sallama ta shiga Ummy kuma naji bata amsa ba, dan haka bata shiga ba saita tsaya daga k'ofar tace "Ummy Ammar kina lafiya? Naga har anyi sallah kuma baki fito ba." Tasowa tayi daga inda take ta zo ta bud'e k'ofa, kallon kallo sukayi sai yanayin damuwa tare da ita, cike da kulawa tace "Ummyn Ammar lafiya ko? Ko ba kya jin dad'i ne?" Saida ta rufe d'akin ta fito ta fuskanceta sai kawai ta d'auketa da wani wawan mari, dafe kumci tayi lokaci d'aya ta saki k'ara, Zeinabu da fitowarta kenan daga sallah taji saukar marin, da sauri ta matso tana kallonsu da mamaki, Nana ma dake kan ajiye abinci a tebur ita ma k'ura musu ido tayi, Inna ma saukar marin taji ta tsaya, ba tare data bari ta d'ago ba Ummy ta nunata da yatsa tace "Wannan shine abinda ke faruwa, bana son munarfici da iyayin tsiya." Tsaki tayi ta bita da harara ta fita harabar gidan, Zeituna data kasa had'a ido da ita saida taga fitarta ta tafi a guje d'akinta, Inna ce ta bi bayanta har d'akinta, tana zuwa ta sameta ta zauna kusanta tace "Amarya kiyi hak'uri, hakan zaman ya gada dama indai ance zo mu zauna to zo mu sab'a ne." Saida ta share hawaye sosai ta kalli Inna tace "Ba komai Inna, ni ai ba bak'uwar zafi bace, kawai ki kwantar da hankalinki." Murmushi tayi tace "Hakane amarya, Allah ya baki hak'uri da juriya, insha Allahu zaki zama fitilar gidan nan da zata haskaka kowa." Murmushi ita ma tayi tace "Ameen Inna." Tashi tayi tace "Ni zan koma wajen aiki." Zata fita daf da k'ofa suka had'u da lieutenant zai shigo, gyara mata yayi ta wuce tana mishi sannu da zuwa, amsawa yayi da mutumtawa kafin ta fice shi ya shigo, da kulawa ya kafeta da ido ganin kamar tayi kuka yace "Lafiya amaryata? Meya sameki?" Da murmushi tace masa "Sannu da zuwa, amma yana ganka a wannan lokacin?" Matso da ita yayi gabanshi yana shafa fuskarta yace "Meya same ki Zeituna?" "Ba komai fa." Ta fad'a tana neman zillewa, sake rik'ota yayi yace "Ni fa ba yaro bane, kinsan da haka?" Kallonshi tayi cike da yamutsa fuska tace "Ciki na ne yake d'an min ciwo, amma kuma yanzu ya daina." "Kin tabbata ya daina?" Cike da tabbatarwa tace "Ya daina." Sakinta yayi ya nufi wajen wata drower dan d'aukar abinda ya kawoshi. *Bayan* sallah la'asar ya gama shiryawa zaije gidan gonar, a falo ya sameta da wayarta a hannu, yana zuwa ya sunkuya ya sumbaci bakinta ya d'ago, kallonshi tayi tace "Sir har ka shirya?" Saida ya shafi k'asumbarshi ya tsaya da kyau gabanta yace "To ya? Nayi kyau ne?" Saida ta mishi da hannu👌tace "Ka had'u ba kad'an ba, sai fatan Allah ya kad'e idon mak'iya a kanka." Murmushi ya mata ya juya yace "Saina dawo." Mik'ewa tayi tabi bayanshi har bakin k'ofa, saida ya sake rumgume ta sannan ya juya zai tafi sai kuma ya tsaya ya juyo, kallonta yayi yace "Kin kira kankana ne tunda ta tafi?" Saida ta d'an bud'a baki tace "A'a." "Me yasa?" Ya tambaya yana kafeta da ido, saida ta turo baki tace "Yah Ammar k'aryata ni fa tayi gaban mutane, bayan kuma nasan bata son tafiya." Saida ya wani tausasa murya yace "To sai me? Ki kirata kiji ya take, kinji ko?" Yana fad'a ya fita ya barta, ciki ta dawo ta d'auki wayarta ta zauna ta kira yer uwarta, a lokacin bata tunanin ganin kiran Amna amma sai gashi ta gani, da farin ciki ta d'auka ta kara a kunne tace "Banyi tunanin zaki kira ni ba?" Daga b'angaren Amna tace "Pourquoi?" Daga kwance Hamna tace "Parce que je sais qui tu est." Murmushi tayi ta gyara zama tana fad'in "Kamar yanda na sanki ba, fad'a min ya kike?" Bata tsaya dogon tunani ba tace "Tante Aissata, elle est très méchante." Dariya Amna tayi tace "Je sais, shiyasa ma na hanaki tafiya dan nasan babu yanda za ayi kiji dad'in zama da ita." Hamna dake kwance a gado tace "Manta da ita kawai zanyi maganinta, fad'a min ya kike?" Saida ta sauke numfashi tace "Lafiya ta lau." Daga b'angarenta murmushi tayi tace "Est ta nouvelle vie?" Cike da farin ciki tace "Bansan ya zan kwatanta miki irin farin cikin da nake ciki ba, ina cikin farin ciki sosai rabin jikina." Da mamaki Hamna tace "Da gaske? Ammar fa Amna?" Dariya tayi tace "K'warai kuwa shi, zakiyi mamaki idan kika ga yanda muke zaune dashi." Zaune ta tashi tace "Amnaaa, anya kuwa? Kamar ya koya miki son shi ko?" Cikin murmushin daya sub'uce mata tace "Si je le te dit la vérité je le te dit oui." Kamar sukar mashi taji a zuciyarta, tsam tayi kamar zata saki wayar, zuciyarta saida ta buga saboda jin abinda ta fad'a, to ita meye makomarta kenan? Tana d'auke da banzan cikinshi fa, ba zai yiwu ba gaskiya, dole tayi gaggawar tsayar da wannan abun haka, ba zata juri jin wannan kunyar ba, jiki a sanyaye Hamna ta amsa mata da "... *Alhamdulillah* *Yawan sharhi yawan rubutu.* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.N.A]* ☆🖊️ _Bismillahir rahamanir rahim_ _45_ "Abun mamaki, na d'auka zaku jima baku saba ba." Murmushi tayi tace "Nima haka." Hamna ce tace "Amma dai kina shan duka da rashin kunya?" Dariya tayi sosai kafin tace "Toi même tu le sais." Fira sosai sukayi cike da kewar junansu kafin daga bisani suyi sallama. Ammar ma fitarshi wajen lieutenant yaje, shi kad'ai ya samu kan makeken lallausan karfet kishingid'e cikin k'ananan kaya yana sha iskar mangwaro dake kad'awa, zaunawa yayi shima yana fad'in "Abba barka da hutawa." Zaune ya tashi yana fad'in "Har ka iso?" "Um Abba." Ya fad'a yana d'aukar roban ruwa ya d'aga kai yana tsiyayawa yasha, saida ya gama ya kalleshi yace "Abba ka ce na zo, lafiya dai ko?" Tank'washe k'afafu lieutenant yayi ya kalleshi a nutse yace "Ammar, ina so ne na sani, meye matsalarka a rayuwa?" D'aga kai yayi ya kalleshi ido cikin ido, kamar mai son fahimtar wani abu sai kuma ya kawar da kansa yace "Soyayya, da kuma k'auna." Mamaki ne ya cikashi sosai na abinda ya fad'a, kallonshi yayi sosai yace "Ban gane ba." Murmushi yayi yace "Ba zan iya cewa komai ba Abba, kayi tunani ka fahimci abinda nake nufi, amma ka sani nayi jarumta sosai da har ban iya gallabarku ba, yara irina da suka rasa abinda nima na rasa wasu su kan kashe kawunansu, wasu su kan kashe 'yan uwansu da ake nuna musu fifiko akansu, wasu kuma su fad'a shaye shaye da tunanin samun mafitar matsalarsu, wasu suna zama 'yan ta'adda ko kuma su fi k'arfin iyayensu, wasu kuma a wayi gari su k'i iyayensu su tsanesu, idan sun girma zasu iya mantawa da su suma, Abba duk abu d'aya yakan iya jawo wannan matsalolin, rashin samun kulawa daga iyayen da suka haifeka, wanda ma basa ganinsu a doron duniya ya suka k'arata bare kai da kake ganinsu kuma sunyi watsi da kai?" Wuri d'aya ya kafe da ido yana kallo da daskarewar tunani ta yanda baya tuna komai a k'walwarshi, jin shirun yayi yawa yasa Ammar kallonshi, murmushi yayi ganin yayi kamar gunki ya rik'o hannunshi, suna had'a ido ba tare daya daina murmushin ba cikin rawar murya mai kama data kuka yace "Abba, ka daina kirana d'an iska bana jin dad'i, bana son kana hantarata musamman a gaban mutane, ina so ka dinga sa min albarka kana min addua'r alkairi." Sakin hannunshi yayi ya sunkuyar da kai, siraren hawaye ne yaji sun taho mishi, hannu yasa ya share ya d'ago ya kalle shi, tausayin shi ne ya kama shi sai kawai ya zuro hannu ya dafa kanshi, sake kallonshi yayi sai kawai zuciyarshi ta karye ya fashe da kuka, cikin tashin hankali ya matso kusanshi ya fara share mishi hawayen yana fad'in "Kai lafiya? Meye na kuka kuma? Yi hak'uri mana kaji, na daina daga yau ba zan sake ba." Tafukan hannaye yasa ya rufe fuskarshi ya kwantar da kanshi kan k'afar lieutenant, daddab'a shi ya fara yana rarrashi, da k'yar ya tsagaita da kukan amma bai d'aga daga k'afarshi ba, sun jima haka kafin ya tashi zaune suka fara hira, sosai suka ji dad'in wannan lokacin saboda hirar fahimtar da sukayi, har ta kai ta kawo lieutenant yana sanar dashi harkokinshi na yau da kullum, k'aratowar magrib tasa su d'aukar makullan motarsu suka bar wurin. *Bayan wata uku* Rayuwa tayi dad'i sosai a b'angaren Ammar da Amna, zama suke na fahimtar juna da girmamawa, duk da kalmar so bata tab'a shiga tsakaninsu ba amma wata kalmar idan ya zage damtse ya mirgino mata ita kanta har kasa d'auka yake, babu kasawa a salon kulawar da yake nuna mata, haka kuma babu kasawa a salon muguntar da yake mata, zamu iya cewa soyayya ce da kuma wahala, yanzu haka har ta saba da muguntarshi, ba wuya zai kai mata k'ulli ko zagi, kuma a take a wurin zai ce ta yafe mishi, dan haka bata sa wannan a matsayin abun damuwa ba.Yanzu haka Allah ya azurtasu da samun k'aruwa, ya rub'anya kular da yake mata, shiyasa ya daina tab'a lafiyar jikinta idan dai ba kashe arna yake ba wanda baya wasa da kashe su. A b'angaren Abba ma yanzu komai yayi daidai, aiki kam lieutenant shi ke abinsa, amma kasuwanci kuma duk ya damk'a ragamar hannun Ammar da Amar, shima kuma Amar yana ganin tashi kalar cutar, sai dai kuma shima ya saba kamar yanda matarshi ma ta saba. Jamila ta gama k'osawa da halin da matar yayan nata take mata, so da dama idan suka had'u saita dinga mata shagub'e da jirwaye mai kama da wanka, tana ninketa ta baibai da wasu maganganun da bata iya gane su ba, ga Huda da take ta k'ok'arin tusata a gurin mijinta ko yaushe, tana hana su shak'at ba dare ba rana, gashi shi kanshi Jibril d'in ta fahimci ya d'an canza daga yanda yake, sai dai har yanzu ta kasa tambayar kowa sai k'unsar bak'in cikinta take ita kad'ai, amma yanzu kam daf take da tayi magana dan abun ya gundureta. Hankalin Ummy ya tashi sosai ganin har anja watanni ba'a maganar dawowar Hamna gidan, hakan yasa kawai ta shiga ta fita har saida ta kasance d'aya daga cikin wanda zasu tafi information a *France* na wata shida, tayi murna sosai dan haka ta kira Hamna ta fad'a mata komai, a wannan rana basu kwanta ba saida Hamna ta samu mafita kan yanda zatayi ta bar gidan nan, ba gidan kad'ai ba duka garin, dan ita kanta tana so ta tafi kafin cikinta ya shiga wata na biyar har a gane halin da take ciki, gashi masifar Aissata ta isheta, jarabar yau daban ta gobe daban, uba kuma ba mai zama gida ba, ko yana garin ma saita kwana ta wuni basu had'u ba ko a tsakar gidan. Cikin ikon Allah ko da ta fad'a ma Gambo tanti *Gishata* (k'anwar Ummy) take neman alfarmar taje *Agadez* (asalin Ummy in baku manta ba) ta dinga kwana a wurinta saboda mijinta baya nan, girman Ummy da kuma kimarta na yanda ta raini yaran yasa bai iya mata musu ba yace ya amince ta tafi, amma karta bari Hajia taji dan zatayi fad'a, dad'i sosai taji na barinta da yayi. Da kanshi yasa dreba ya d'auketa sai Agadez inda suka had'u da Ummy anan ita ma da shirin tafiyarta. Gishata tayi mamakin ganinsu lokaci d'aya, bata sare ba saida Ummy tace France zasu je, tambayarsu tayi sai Ummy tace kawai tayi hak'uri idan sun dawo zasu fad'a mata, amma ta musu alk'awari d'aya shine ko wani ya tambayi Hamna karta nuna ta san inda take, sannan ita ma Ummyn bata so kowa yasan ta zo, hankalinta ya tashi da tunanin abinda ke faruwa, amma sai Ummy tace tayi alk'awarin fad'a mata komai idan suka dawo, sannan kad'ai ta d'an nutsu tare da musu fatan alkairi a sanda jirginsu zai d'aga, wanda hatta passeport da visa duk Ummyn ta d'auki nauyinsu a kanta. Tasan kuskure take aikatawa, amma ta riga da ta bar gini tun ran zane, gashi dalilin kuskuren da d'anta ya aikata yau ta wa mijinta k'arya cewa wata hud'u zatayi, dan farko bai so tafiyar ba ko kad'an saboda cikin da yake tunanin tana da shi, da k'yar ta shawo kanshi ya barta da tace wata hud'u ne kawai, gashi shima dalilin k'aryar data mishi har saida ya fad'awa Alhaji ya ma Hajia magana kan a barta ta tafi, ita kam yau ina zata saka kanta ne?. Tafiyar Hajia saoudia abubuwa sun rage yanda kowa ke abinda ya so, Alhaji dai dama ba mai zafi bane ko tsanani, shi kai ko fad'a ma da wuya kaga yana wa mutum, mafi yawan lokaci ko ya wuni gidan zai wuni a cikin jardin (guardin) ne, ko kuma wajen wasu harkokinshi na daban, amma yau daya zama zata dawo duk sai jikin kowa yayi sanyi, masu girki sun baje bajintarsu duk dan su faranta mata, sai dai duk da haka sun had'a da addu'a kan Allah yasa ta so abinda suka mata ba tare da tayi k'orafi ba. *Ta farka* ne saboda fitsarin daya cika mata mara, zaune ta tashi cike da kasala kafin ta yaye zanin rufar ta sauka ta shiga ban d'aki, saida ta rintse ido saboda zafinda take jin sanda take fitsarin, tana kammalawa ta kara ruwa da na d'umin da take ajiya kafin ta fito, sai lokacin ta iya jin sanyin dake akwai wanda hakan ke nuna lokacin sanyin ne zaiyi, sake komawa tayi kan gadon ta kwanta taja zani ta rufa ruf, har zata gyara kwanciya taji ya jawota jikinshi ido rufe yana fad'in "Me zakiyi da abun rufa bayan gani? Ni ne gadonki kuma abun rufarki." Tashi yayi ya mata runfa ya had'a goshinshi da nata yana kallon idonta yace "Kina lafiya duniyata?" Saida ta sakar masa murmushi tana lumshe ido tace "Lafiyata lau duniyata, bacci kawai nake ji, yaron nan naka baya barina bacci saboda yawan tashi fitsari." Dariya mata yace "Ki barshi lokacinshi ne yayi, idan kuma kina so idan kina jin fitsarin ki dinga tashi na saina tsotse miki shi." Cikin dariya ta yamutsa fuska tace "Ta yaya?" A hankali ya fara yin k'asa yana d'aga rigarta sama dake iya gwiwanta yana fad'in "Kamar haka." Saida ya tabbatar ya cire rigar daga jikinta da wandon rigar, zanin rufar yaja musu ruf yayin da ya fara bata kulawa yana tsotse mata fitsarin🙈 (Sis Chappa karki karanta wurin nan zuciyarki zata buga), cikin k'ank'anin lokaci ya gama rikita mata lissafi yana neman gangarawa, Allah ya sani baya gajiya da ita, sai dai duk da haka bai iya manta daren farkonshi da yar uwarta ba, wannan daren na musamman ne a wurinshi, amma Amna fa ba baya bace ita ma wajen gamsar dashi kamar yanda yake so, jin yana saisaita manyan kayan zai turasu babban birni yasa ta d'ago da kanshi ta kalleshi cikin shagwab'a tace "Yah Ammar, bacci nake so nayi fa." Saida ya sumbaci kumatunta tare da da saka mamanta a bakinshi yace "Ai shi salon yaki iri iri ne, wani magaucin naka zai fi kyau ka masa shigar dare, wani kuma shigar safe ta dace dashi yanda zaku ga juna ga da ga, ina so na kashe mak'iyina ne wanda suke son min kutse a cikin dare saboda tunanin bacci nake a wannan lokacin." Bushewa tayi da dariya ta k'ara jawo kanshi ta d'ora bakinta kan nashi tace "Kai na musamman ne jarumin mijina." Had'e bakinsu tayi ta shiga tsutsa tana wasa da harshenshi yanda tasan yafi so, numfashi ta sauke mai k'arfi tare da sakin bakinshi saboda yanda ya shigar da kanshi jikinta, yana fara hak'arta ta kalleshi tace "Yah Ammar, ina son zama da kai, na fahimceka mijina, a baya muna maka kallon wani mugu, ashe duk dan bamu zauna da kai bane, ka yafe mana dan Allah, *ina sonka* sosai." Wani k'arfi ne yaji da yasa shi k'ara gudu da aukin abinda yake yi, bai ce mata komai ba ya ci gaba da aiki tuburan, saida yayi lak'was kafin ya saka harshenshi cikin kunnenta yana d'an wasa dashi ciki, ya jima yana mata haka har bacci ya fara ridarta taji yace "Nima haka, *ina sonki*, ni naki ne ke kad'ai kamar yanda ke ma tawa ce ni kad'ai, Amna ko bayan raina zaki ci gaba da zama tawa, idan kuwa wani yayi k'ok'arin rab'ar inda kayana suke, to wallahi zanyi fatalwa na addabi kowa, ke ba wai ke da shi hatta wanda suka halarci d'aurin aurenku sai sun shiga dubu uku, kinji ko." Bushewa tayi da dariya sosai ta ture shi daga jikinta ta tashi, ban d'aki ta shiga ta had'a ruwan d'umi dan yin wanka, yana shigowa ya gani yace "Ruwan zafi? A wannan lokacin? Kina matar soja kina jin sanyi." Juye ruwan yayi a banza hakan yasa taja baya tace "Allah yah Ammar ba zan iya dasu ba sanyi nake ji sosai." Jawota yayi da tsiya yace ai sai tayi ko bata so, da k'yar da lahaula ta d'anyi wankan sama sama mai had'e da alwala, tana idawa ta mik'e zata jawo towel ta fito ta barshi ya rik'eta, saida ya tsaya da ita gaban dogon panpo ya kunna musu ruwa, saida ta zabura zata ja baya ya rik'eta ya rumgumeta a jikinshi, tun daga saman kai har k'afafu ruwan ke saukar mata, haka yasa ta rirrik'e shi gam ta danna kanta cikin k'irjinshi sai numfashi da take a hankali baki bud'e, saida ya tabbatar ya gama abinda yake kafin ya d'aura towel a k'ugunshi ita kuma ya sumgumeta hakanan ya fito da ita, ajeta yayi tsaye yace "Karki saka kaya ina zuwa." Ko da taji haka tasan me yake nufi, kenan zata kwana babu kaya ko? Tana kallo ya d'auke zanin gadon ya d'auko wani zai canza, yana idawa ya zo inda take ya kamata suka nufi gidan yana fad'in "K'anwar kankana kenan sarkin ruwa, ke fa kamar gulbi kike." It dai k'ala ba tace ba sai son ta ganta cikin zanin rufa ta rufe, suna kwantawa ya k'amk'ameta sosai suka lullub'a cikin zanin nan yana ta ci gaba da wasa da jikinta, ba wuya bacci ya d'auketa shi kuma yana ganin haka ya tashi ya je d'akinshi ya sako doguwar riga ya dawo, sallah ya kabbara bai kuma jima da farawa sai aka fara kiran sallah asuba, saida yaje masallaci yayi sallah ya zo da niyyar tashinta, yana shigowa ya ganta ta fito tayi alwala ita ma. Tunda sanyi safiya sosai mota uku ce ta rako Hajia zuwa gida, duk gidan na wasar baki na ganinta wanda bai kai ciki ba, kowa yaje ya kwashi gaisuwa da yi mata sannu, sai da rana ta fito sosai sannan ta fito waje, kaf saida ta zagaye gidan tana duba abinda aka b'ata dan anga bata nan, haka ta dawo falonta nan ma ta ga komai yana yanda yake sannan ta zauna, lokacin ne Maryama ta shigo gaisheta tare da Huda a bayanta, Hajia na ganinta ta sake d'aure fuska, har suka k'araso bata daina mata wani banzan kallo ba, ita ma cikin rashin kunya a tsaye ta kalleta tace "Anzo lafiya?" Wani kallon kin ma rainani ta mata tace "Ban fad'a miki bana son ganin wannan shegiyar 'yarta ki a falona ba?" Fuska a had'e tace "Shegiya kuma? 'Yar tawa?" "Eh 'yar taki, ko kin manta hanyar da kika sameta ne?" Saida tayi wata tsayuwar rashin mutumci kafin tace "A gaskiya Hajia bana so ana kira min 'ya da shegiya, idan ba haka ba fa akwai matsala." Gyara zama Hajia tayi zatayi magana sai Zeinabu dake nesa dasu tace "Ke Maryama, yanzu Hajia zaki wa rashin kunya, wai ke wace irin fitsararra ce ne?" Kallon Zeinabu tayi tace "Ki shinshina kiji mana, kunga nifa gaskiya ba zan d'auki wannan wulak'ancin ba, haka kawai daga shigowa gaisheki sai ku hau mutane da jaraba." Zeituna da fitowarta kenan daga madafa ne tace "Maryama, shin bai ci ace kin girmama mutanen nan ba duba da matsayinsu a gurinki." Husseina dake zaune kan d'aya daga cikin kujerun teburin cin abinci ce tace "Ke Maryama ya isa haka, wuce ki koma d'akinki bana son hayaniya." A hassale ta kalli Zeituna tace "Wane matsayi? Wane matsayi garesu gare ni? To idan ni na tuna su ki tambayesu suna tunawa da hakane? Sam basa kallona da mutumci saboda karuwa ce ni, to ai kunsan da haka kuma kuka barshi ya aureni." Daga zaunen nan Hajia tace "Yayi marar kunya, to dama wa zaiyi tsammanin ki girmama shi a gidan nan duba daga inda kika fito, sannan ki sani wallahi da Junaid ya bi ta tawa da ko a hanya ya ganki saiya tofar da yawu, dan haka yanzun nan ki fitar min a falo tare da shegiyar 'yar nan ta ki." Cikin jin zafin maganar Maryama tace "Shegiya? To kuji da kyau Nurul Huda ba shegiya bace, ita ma nan gidan ubanta ne kamar yanda kowane yaro ko ganin gidan ubansa ne nan, wallahi ko aure na da Junaid ya k'are ni zan bar gidan nan amma banda ita." Wani kallon marar hankali suka bita dashi dukansu kafin Hajia tace "Au! Wai dama rashin hankalin naki har ya kai haka? To yaushe yayi adapténta a matsayin 'yarsa? Kina da hujjar anyi haka?" Ita ma wani murmushin baku da hankali ta musu tace "Ba ina nufin gidan uban bogi ba, uba mahaifi nake nufi wanda ya haifeta, wanda ta fito ta tsatsonshi." Sallama Junaid yayi wanda ya shiga can bai sameta ba ya shigo nan, da sauri Hajia tace "Yawwa k'araso, zo ka fad'a mana yaushe wannan aljanar yarinyar ta zama 'yarka?" Murmushi tayi tace "Zaku jijjiga idan kuka ji ubanta na asali a gidan nan." Sororo Zeinabu tayi, tunaninta d'aya shine Huda yar Junaid ce, kenan hakan na nufin *tarihi ya maimaita kansa*? Junaid kuma da baisan kan maganar ba kallon Maryama yayi yace "Bani na haifeta ba Hajia, kawai dai ina matsayin ubanta ne." Murmushi tayi ta kalli Maryama tace "To kinji meya fad'a? Dan haka ki sani ko da zai mayar da 'yarki a matsayin 'yarsa dole saina yarda da hakan kafin yasa hannu a takardar sheda." Zeinabu ta fara kallo kafin Hajia tace "Ina so daga yau kar a sake kira min 'ya shegiya alhalin tana gidan ubanta, idan ba haka ba wallahi duk saina tono shegun gidan nan in ya so ayi duk wacce za ayi, Junaid dama na aureshi ne dan shi ya matsa sosai, ko da na bar gidanshi ba zanji zafi ba, dan har yanzu sana'ata na nan na jirana na d'ora daga inda na tsaya." "To sai me? Ki koma kasuwancinki mana ni kuma a randa kuka rabu dashi a ranan zan d'aura masa aure da wata, dan in tabbatar miki ke banza ce wallahi." Cewar Hajia a hassale ita ma, tab'e baki tayi tace "Amma ki sani ba zai so zab'inki ba kamar yanda ya so ni." Juyawa tayi ta fita, shi Junaid kawai mamaki yake, ashe dama haka take? Lallai zuciya bata mana adalci da take samu son wanda basu dace damu ba, ya juya zai bita Hajia tayi tsaki tace "Malohon banza, yarinya k'arama ta tsaya tana fad'a min magana a matsayina na uwar ubanka amma kana saurarenta, ai ko da ni baka sona ba za iya mayar mata da martani ba saboda ni kayi dan uwarka ma." Saida ta kawar da kai tace "Hum! Shiyasa ake cewa kowane kare da ranar sa, yau da Ammar ne matarshi ta tsaya tana fad'a mana magana, wallahi ko 'yar sarkin Istanbul ce ita saiya zabgeta da mari sai dai a d'aureshi ko a kashe shi." K'ala baice mata ba yayi tafiyarshi haka ma Zeinabu barin falon tayi, yana fita d'aki ya sameta zaune sai cika take, cikin fad'a yace "Mari ashe baki da mutumci? Uwar tawa da kakata kika gurzawa wannan rashin mutumcin? To wallahi ya zama na k'arshe, inba haka ba zan miki abinda zakiyi mamaki, dan ba zaki mayar dani sakarai ba." Ya juya zai fita ta mik'e tace "To indai hakane ka fad'a musu kar wanda ya sake kiranta da shegiya, nan gidan ubanta ne ita ma, kuma a shirye nake da na bar gidan nan amma ita tana nan duk da bata da gadon ubanta." Murmushin ko dai bata da hankali ya mata yace "Mari ban miki musu ba cewa ina kallon Huda kamar 'yar dana haifa, amma ba hakan zaisa ki ce nine uban ta ba." Ita ma murmushin ta masa tace "Karka damu Junaid, da sannu zaka san waye ubanta indai har kakar can taka tana sarar kiranta shegiya." Bai kula da abinda ta fad'a ba kawai ya bar gidan, *da yamma* kuma Jibril ke samun labarin abinda ya faru wajen Husseina, hankalinshi ya tashi sosai, dan haka daya shiga b'angarensu saiya fara wucewa b'angaren ta, Huda dake zaune k'ofar shiga tana wasa yace ta kira mishi ita, bayan ta fito ne rai b'ace yace "Maryamaashe baki da hankali? Akan me zaki musu rashin kunya saboda kawai kina ganin kina da wani sirri a hannunki, to dan Allah in kin cika babbar karuwa kije ki fad'a, ki fad'a sai me? Huda 'yata ce kuma na yarda zan karb'eta, amma kisan wani d'aya shine nima gado nayi, kinsan ko a wurin wa?" Wani kallo take binshi da shi kamar bata fahimtar abinda yake fad'a, murmushi yayi yace "A gurin kakana mana, ko kuma nace kakanmu ni dake wato malam Rabi'u." Saida ya had'e fuska ya nuna ta yace "Idan kika bar min Huda anan to ki sani Labaran ma zai koma wajen nashi uban, tunda abun babu mutumci." Sama da k'asa ya bita da harara ya nufi hanyar b'angarenshi yana fad'in "Yar iska kai duk ki d'aga hankalin mutane, to kaina farau shiga gonar da bata hallata gareka ba." Da kallo ta bishi, malam Rabi'u, kuma Labaran? Yana nufin malam ne ya haifi mahaifinshi? Kai ia ba zai yiwu ba? Malam daya tsani zina, dalilin da yasa kenan bata nemi taimakonshi ba sanda tayi ciki, dan tasan zai iya kasheta ma da duka, sai yanzu a nuna mata babban mutum kuma uba ace d'anshi ne, to ta yaya? Da wannan tunanin ta koma ciki ba tare data gamsu da abinda ya fad'a ba. Yamma lik'is Amna ta shigo b'angaren Hajia, kai tsaye wajen Husseina ta nufa, har d'aki ta sameta tace "Hajia dan Allah ba kiyi ajiyar yakuwa ba?" Dariya ta mata tace "Uwar kwad'ayi, akwai amma busassa ce tana madafa." "Yawwa, ina zuwa." Ta fad'a tana nufa madafa, tana zuwa ta samu Zeituna suna aiki, ko da ta fad'a mata abinda ta zo yi tace "A'a koma duniyar Ammar, ki bari zan d'ora miki ita a wuta." Saida ta rumgumeta ciki da shagwab'a tace "Nagode uwarmu, Allah ya barki ke da ubanmu." Da murmushi kawai ta bita ta fita, tana fita ta d'ora mata, kafin ta tafasa ta gyara kayan had'inta, Amna kuma jin an fara kiran sallah yasa tayi alwala a d'akin Husseina tayi sallah, tana idarwa ta cire hijabi ta mik'e da niyyar zuwa ta gyara, sai ga Zeituna ta shigo da wata roba mai kyau ta mik'a mata tace "To aci lafiya duniyar Ammar." Dariya tayi tace "Kai aunty Zeituna kin dai rik'e wannan sunan ke ma." "Kamar yanda kike rik'e sunan uwata ba." Ta fad'a da dariya, bud'a robar tayi tace "Lahh! Aunty Zeituna yanzu gyara min kikayi?" "Mun gama aiki ne da madafar za'a rufe sai kawai na k'arasa miki." Tana fad'a ta juya tana fad'in "Na tafi nayi sallah nima." "Nagode aunty Zeituna." Murmushi kawai tayi ta fita, ta zauna ta d'iba ta kai bakinta, wani masifar dad'i taji kamar zata tsinka harshenta ko yawu zasu dalolo mata, hannu tasa zata k'ara kaiwa Ammar ya shigo da sallama d'akin Husseina, Husseina data sallame ce ta amsa tare da Amna, yana k'arasa shigowa ta bud'e mishi hannu d'aya alamar ya rumgumeta, sunkuyowa yayi ya rumgumeta tare da manna mata suma a baki yana kallon kwanon hannunta, Husseina ya kalla yace "Hajajju anwuni lafiya?" "Lafiya lau, har an sauko?" Ta fad'a da raha, bai iya amsa mata ba sai Amna da yace ma "Menene kike ci da yasa kika baro can?" Shagwab'e fuska tayi tace "Duniyata yakuwa?" Zaro ido yayi yace "Ya me?" Baki sake ta sake cewa "Yakuwa." Da k'arfi yasa hannu ya fizge robar yace "Ubaki ma, Allah baki cinta sai kace wata mayya, kina da k'aramin cikin ne zaki ci wannan abun." Cikin kuka ta tara mishi hannu tace "Dan Allah yah Ammar taimaka ka ban kar yawuna su k'are." "Sun jima basu k'afe ba, Allah ba zan baki ba." Kallon Husseina tayi tace "Dan Allah Hajia ki ce ya bani, ina so na ci." Da sauri ya fito da waya daga aljihu kawai ya d'ora a kunne ya juya zai fita yana fad'in "Hello, Hello, kai bana jinka." Tsaf ya fice dan kar Husseina ma tayi magana, dariya ta mata tace "Kin gani ko, dan haka ki hak'ura kawai." Girgiza kai tayi tace "Je ne peux pas wallay, bari na same shi." Dariya ta mata tace "To kije, kinga idan da rabon kisha mari sai ki dawo kina kuka." Tsayawa tayi daga d'aukar hijabin tace "Kuma fa hakane? Ba zai dakeni ba Hajia ai yanzu ya daina." Saka hijabin tayi ta fita da sauri ta nufi b'angarensu, tana zuwa ta same shi zaune sai k'ara kallon yakuwar yake yana b'ata fuska, yana jin shigowarta ya d'aga kai ya sauke mata idonshi da suka bayar da yanayin k'araso na ci ubanki, cak ta tsaya tana kallonshi da tsoro tana d'an cukuikuye hijabinta, hannu ya tara mata tare da nuna mata cinyarshi yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.N.A]* ☆🖊️ _Bismillahir rahamanir rahim_ _46_ "Zo zauna nan." Saida ta k'ara yin kalar shagwab'a sosai kafin ta fara takowa a hankali tana nufoshi, k'ank'ance idonshi yayi yana mamakin k'arfin halinta, tasan fa idan ta zo me zai mata, tasan saiya mintsineta ko ya mata wata muguntar, amma duk da haka ta taho kuma a madadin ta koma ko ta nemi wajen b'uya, baisan lokacin da murmushi ya sub'uce masa ba, tabbas k'arfin hali da jarumtarta sun birge shi, ta nuna mishi zata iya hak'uri da shi duk abinda zai mata, kafin ta k'araso sai kawai ya ji babu buk'atar ya mata abinda yayi niyyar yi. Cike da tsoron nan ta zauna akan cinyarshi ta rufe fuskarta ko da ya kan iya kawo mata mari ko ja mata hanci ya matse shi, a hankali ya janye hannayenta yace "Kalleni mana, tsoro kike ji?" Girgiza kai tayi ba tare data bud'e ba, yana kallonta shima yace "To in dai hakane kalleni." Bud'ewa tayi ta kalli fuskarshi amma ba cikin idonshi ba, aje robar hannunshi yayi kan k'aramin teburin yana kallonta yace "Fad'a min duniyata me kike so?" Robar hannunta ta nuna mishi tare da turo leb'enta na k'asa gaba na sama kuma ta shigar da shi ciki sosai, kallon robar yayi sannan ya kalleta yace "Amna bana son irin wannan ciye ciyen fa, da zogale ce ma tafi anfani a jiki, ki bari gobe da safe na miki alk'awarin zan samo miki zogale kinji." Yanda tayi da fuskarta yasa shi sumbatar kumatunta dan tayi fayau da ita tayi kyau sosai, shafa kumatun yayi yace "Kiyi hak'uri kinji, ai kin yafe min ko?" Cikin shagwab'a wai ita ga auta ta kama hannunshi dake kan fuskarta tasa babbar yatsarshi baki tana tsutsa, murmushi yayi yana d'an girgiza kai yace "Autar Tanti kenan, rigamar dai ta motsa ko? To fad'a min me zan miki da zaisa ki hak'ura." Cike da sangarta tace "Ni kawai ka ban na ci wannan, shi nake so na ci, kuma ai ba laifina bane na beby ne." Cikin muryar dake isar mata da sak'on kiyi hankali fa yace "Amnaaa." Da sauri tace "To kawai ka siyo min kankana." Rugugugu! Sautin da gabanshi ya bayar kenan sanda ta ambacin sunan kankana, nisa dashi da tayi da kuma samun Amna sunyi tasiri sosai wajen mantar dashi ita, amma kuma bai kamata ace ya manta da ita ko dan abinda ya aikata mata, to amma ya zaiyi? Dole ya manta da ita tunda dai babu komai tsakaninsu, ciki ne dama yake zargin tana da kuma da akwai ciki da yanzu ya bayyana kowa yaji, dan baya tunanin Ummy zata iya yin abinda tayi yanzun, jin ta sake saka hannunshi a baki tana tsutsa yasa shi dawowa hayyacinshi, murmushin yak'e ya mata yace "To bari nayi wanka sai mu tafi tare." D'agata yayi daga jikinshi ya nufi hanyar d'akin kwananshi, tsayawa yayi ya juyo yace "Amma ke da baki shan kankana?" "Haka kawai nake sonta yanzu." D'akin ya nufa yana fad'in "Kinyi waya da kankanar asalin?" Cikin d'aga murya tace "Eh, tana lafiya." Bayan isha'i suka fita, haka kawai suka dinga yawo suna zaga gari, sun jima sosai kafin ya mata siyayyar kayan ciye ciye suka dawo gida, tana fitowa daga cikin mota ta d'an matse cikinta tace "Wash." Kallonta yayi sanda yake fitowa yace " Ya dai?" Duk da abune da take wayan ji amma hakan baisa ta iya fad'a masa ba sai kawai tace "Ba komai, cikina ne ya d'an juya." Tsaye yayi har ta zagayo wurinshi ya kama hannunta yace "Ki kula fa Amna, karki ja min asara ki sani sabon aiki." Dariya kawai tayi suka nufi b'angarensu, saida ya tabbatar ta nutsu harta kwanta sannan ya zo ya ga Abba suka tattauna kafin daga bisani sukayi sallama. *Washe gari* da safe kusan duk familyn ne a falon kowa da wanda ya zo ya gaisar, Ammar ma suna kusa da Zeituna zaune shi da Amna, da k'yar Junaid ya matsa mata ta zo gaishe da mutanen ba dan ta so ba, shiyasa ma ko da ta shigo ko sallama ba tayi ba, tana kallo yana gaishe da kowa amma banda ita, ganin hakan yasa Ammar k'ura mata ido, ko shi dai ai yana gaishe da kowa da girmamawa, amma tsabar rashin kunya ita ba sallama kuma ba gaishe da mutane, ba fa zai d'auka ba, wannan iskancin ba za'a yi shi dashi ba. Junaid na juyowa inda yake dan su gaisa ya kula da kallon da yake mata, cikin dubara ya d'an ja gyalenta suka koma gefe, juyawa tayi zata fita Junaid ya bita da kallo, Ammar daya kula da kowa na wurin ya bita da kallo amma babu mai k'arfin halin da zaiyi magana yasa shi kallon Junaid yace "Matarka raina mutane ne tayi?" Ido a tsaitsaye ya kalleshi fatanshi kawai su rabu lafiya, ita kuma juyowa tayi tana mishi wanni kallo tace "Kamar ya?" Saida ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yace "Naga kamar kinfi k'arfin ki gaishe da mutane, me kike ji dashi to?" Cike da rainin tace "Ina da wani abu d'aya a rayuwata, duk ta yanda aka zo min haka nake zuwa nima, an nuna min ba'a k'aunata a gidan nan, shiyasa nima ban nuna ina k'aunar kowa ba." Idonta ya kalla yace "Amma ai kinsan girmama mutum ko? Sannan nan ba gidanki bane ko na mijinki, dolenki ki girmama duk wanda kika gani a ciki inhar kina da mutumci." Murmushi ta masa ta rumgume hannaye a k'irji tace " Idan kuma bana da mutumcin fa?" Mik'ewar da yayi tsaye yana d'an nad'e hannun rigarshi yasa Zeituna mik'ewa tana kallonshi tace "Dan Allah rabu da ita kaji, bata gajiya da rigima da kowa." Kallon Zeituna yayi yace "Um um uwa barni, ina so ne na fad'a mata da yaren da zata fahimta, duk rigimar da take muku ai dan bata samu daidai da ita bane, ni ba ita zan tsawatar ma ba mijin nata zan dallawa mari a gabanta ta gani, hakan zaisa ta shiga taitayinta." Kallon Junaid yayi rai a b'ace yace "Yo ba dan ma ya d'auki mutane 'yan iska ba har wacece wannan yarinyar da zata zauna tana mana fitsara, yaushe ta shigo gidan naka har ta fara baka kulawar da kake ganin ta isa ta taka iyayenka kuma ta zauna lafiya, to in kai ka zama fanko wallahi ni akan iyayena babu yar iskar data nemi ta raina min su kuma na kalleta, dan ubanta kuma ta jaraba ta gani idan ban fizgo hanjin yarinya ba ta baki, to miye a cikin ido banda ruwa." "Da kyau Ammar, nagode, ka tabka rashin mutumcinka yau Hajia Zeeya'atu na bayanka, tunda shi gindinta ya mishi shamaki da zuciya." Kowa saida ya kalli Hajia da tayi maganar nan, Amna sagale ta kalle ta wacce ta tsargu da abinda ya fad'a take jin kamar da ita yake tunda dai ita ce matarshi, Ammar kuma a ranshi yace "Tunda rashin mutumci ne kenan kin d'aure min gindi? To na fasa." Maryama ce tace "To sai me? Ka mari mijina a gabana ka gani, wallahi da nima saina tsinke matarka da mari kuma a gabanka naga me zai faru." Juyawa yayi ya kalli Amna dake zaune ya tintsire da dariya ya nuna Amna yace "Ke wannan? Jar bala'i! Wallahi kuwa da kinja yau kowa ya kwana da yunwa, ke ki bar bala'i yayi kwana kinji, bana fad'a da mace ni sai maza mazan ma wanda suka k'osa, idan kuma kika cikani sai dai nasa 'yar aljannata ta d'aukar min ke ta cilla a garu." Cikin taushin murya Amar yace "Dan Allah d'an uwa ka rabu da ita." Kallon Maryama yayi ita ma yace "Gaskiya baki kyauta ba, banyi tsammanin haka daga gareki ba." Zaune Ammar yayi yana kallon Amar yana fad'in "To dama me kake tsammani? Baka ga kakan nan nata ba mai masifar fad'a kamar Hajiar gidanmu." Amar da suke kallon juna ne ya mishi alama da ido cewa Hajiar fa na kallonka, duk da ya fahimci me yake nufi sai kawai ya gyara zamanshi ya ci uwar fuska kamar bashi ba, Husseina kad'ai ta iya fito da dariyarta amma sauran duk sun gimtse ta su, Hajia da kamar ta fashe ce tace "Shiyasa ba ma tab'a zama lafiya ni da kai, ba dai nice mai masifar fad'a ba? Zaka gani, akwai ranar da zaka nemi kaji ma fad'an nawa amma na maka nisa." Kallonta yayi fuska a had'e yace "Haba Hajiata, raha ce fa kawai, ke kinsan dani dake bata b'acewa, fad'an ki ai ni jinshi nake kamar kukan tsintsaye matuk'ar dad'i a kunne." Maryama dai basu ma san lokacin data fita ba tare da Junaid, yau ma fad'a sukayi sosai saboda yaji zafin abinda Ammar ya mishi, kuma yasan gaskiya ya fad'a mishi shiyasa ma bai biye mishi ba, amma fa daya mare shi da sai dai cikinsu d'aya ya kashe wani, yanzun ma k'ara fad'a mishi tayi dan sam zaman gidan nan nashi ya fice mata a rai, bata damu ta bar gidan ba tunda kowa na gidan baida mutumci a cewarta. *Misalin 09:00* na safe Tanti Hadiza ta zo gidan, babban falon ta fara shiga cike da fargaban kalaman da zata ji daga Hajia, a lokacin tana d'akin Alhaji dan haka ta samu tarba mai kyau daga su Zeinabu da Soueiba da kuma Zeituna da bata tab'a ganinta ba ido da ido sai yau, a falon suke suna ta hira ta yaushe rabo inda suka cika mata gabanta da abun sha da ci, fitowar Hajia yasa duk wannan farin cikin ya b'ace kowa ta kama jikinta, duk da ta gane wacece amma bata wani kulata ba ta kalli Zeituna tace "Zaman me kuke anan? Ina ce aiki kuke a madafa." "Eh Hajia." Ta fad'a tana mik'ewa ta nufi madafar, su Zeinabu ma mik'ewa sukayi inda Hadiza ke mamaki da maganar zuci cewa "Har yanzu bata canza ashe, yaushe matar nan zata daina bautar da matan 'ya'yanta? Allah ya kyauta." Daga tsaye take k'are mata kallo sama da k'asa, murmushin gefen labb'a ta mata ta kawar da kai daga kallonta tana danna wayar hannunta tace "Wani ko a cikin kaskon mai ka saka shi haka zaka ciro shi a tsiyace, ank'i d'ana ba, amma sanyin ac da abincin gidanshi kad'ai ya isa ya gyara maka jiki." Nufa tayi kan kujerarta ta zauna k'afa d'aya kan d'aya tace "Ina manta wani abu fa, wasu haka suke zuwa duniya a wahalce kuma su koma babu nasara." Ita ma murmushin tayi wanda bai fito da hak'oranta ba ta mik'e tana kallonta tace "Ina kwana Hajia." K'ala ba tace mata ba dan haka ta juya zata fita sai kuma ta kalleta tace "Ba wai zama a cikin daula bane ke nuna kayi nasarar zuwanka duniya, ni a gurina nasarar da soyayyata ma tayi ma nasara ce, wasu basa da sa'ar zama da wanda suke so, ni kuma yanzu haka ina cikin farin cikin da na tabbatar sauran matan gidan nan basa cikinshi, idan kuma k'arya na fad'a ki tambayi kowace kiji zata fad'a miki indai har gaskiya zasu fad'i." Cikin ladabi ta sake kallonta tace "Kiyi hak'uri abisa abinda ya faru, ganin Amna na zo wacce kullum ke min k'orafin ban zo naga gidanta ba, kuma tace gidan jikin wannan yake shiyasa na lek'o mu gaisa kar nima na watsar daku kamar yanda kukayi, ko ba komai ina da 'ya'ya a gidan nan." Fita kawai tayi ta barta, tana ganin gidan tasan shine dan haka kawai ta shiga, sallama ta dinga rafkawa har Jamila da Amna suka lek'o su da su kafi kusa, dukansu rumgumeta sukayi da farin ciki, Amna har kuka tayi na ganin mahaifiyarta, haka suka shiga ciki ta zuba mata kayan tab'awa inda suka bud'e shafin hira, a k'alla awanta uku kafin ta tashi suka shiga wajen Umaimah da Maryama suka gaisa, data fito zata tafi a lokacin Amna ke cewa "Mama ki jira yah Ammar yanzu zaki ganshi tunda na fad'a mishi kin zo, ba zaiji dad'i ba idan ya samu kin tafiyarki." Dariya ta mata tace "To ni dashi kusan kullum ba muna had'uwa ba, kowace juma'a fa sai yaje madarunfa." Zaro ido tayi tace "Mama kowace juma'a? Amma shine bai tab'a fad'a min ba." Dariya tayi zatayi magana sai gashi ya shigo da makullin mota a hannu, da farin ciki da ladabi suka gaisa kafin yace "Tanti har kin fito ne? Amma ai baki jima ba." Da murmushi tace "Haba dai ina laifi ai na jima anan, zan wuce can gida ne wajensu Inna zuwa bayan sallah la'asar kuma saina koma." "Amma kun gaisa da mutanen ciki kuwa?" Saida tayi dariya ta kalleshi tace "Mun gaisa, harda kakarka ma." Dariya yayi shima yace "Ashe kunsha hira." Dariya tayi kafin ta kalli Amna tace "Ki koma ciki ni zan tafi, sai kuma na sake dawowa ganinki ko auta." Cikin shagwab'a ta kwantar da kanta a kafad'arta tace "Mama yaushe zaki dawo?" Kallon Ammar tayi da tunanin abinda zata fad'a mata sai kawai yace "Sai kin haihu mana zata dawo." Kunya ce tasa Amna k'ara sunkuyar da kanta tana murmushi, Tanti kuma a ranta tace "D'ana kenan, anyi halin ba ." Ammar ne yace "Muje tanti saina ajeku." Kallonshi tayi tace "A'a haba daka barshi ma, watak'ila akwai abinda kake wannan shirmammar ta taso ka." "Ku zo muje kawai, ai babu abinda yafi mana ku." Ya fad'a yana nufa hanyar fita, rik'eta Amna tayi sosai wai babu inda zata je, abu da gaske sai kuwa tasa kuka ita sai dai ta tafi da ita, ita ma rumgumeta tayi tana fad'in "Saurare ni auta, kina ji na da kyau?" Kai ta d'aga alamar eh, cikin fitar da kowace kalma take fad'a mata "Kiyi hak'uri ki koma d'akinki ki zauna, na miki alk'awarin zan sake dawowa ba da jimawa ba, wannan kukan yasa dama tun farko ban zo ba, amma idan kikayi shiru yanzu to zan sake dawowa kuma na taho miki da abinda kika fi so, zuwa lokacin nasan Hamna ta dawo kinga ita ma na ganta." Turo baki tayi tana d'aga kafad'a da fad'in "Um um, um im, ban yarda ba ni gaskiya, kuma Hamna ma wa yasan ranar dawowarta." "Au ba zaki hak'ura ba kenan?" Cikin turo baki tace "Na k'iya." "Shikenan to nasan maganinki." Ta fad'a tana kallon inda Ammar ke tsaye, cikin d'aure fuska tace "Yarona zo ka min maganinta tunda bata jin rarrashi." Takowa ya fara yi da k'arfi yana fad'in "Ai kuwa tanti bari kiga yanda zanyi da 'yar banza." Takalmanshi ya ciro yana shirin wurga mata da gudu ta koma d'aki tana rusa kuka, dariya suka saka mata inda tanti tace "Ai maganinki kenan, da kin kwantar da hankalinki da munyi sallama cikin farin ciki." Suna nufa k'ofa Ammar yace "Tanti karki damu, insha Allahu zan kawo miki ita tayi sati d'aya, dan yanzu ta fara kumburo min baki kenan har illa masha allahu indai ba ganinki ta sake yi ba." Dariya tayi tace "Auta ce ku barta tayi rigimarta, amma zaka iya barinta tayi sati d'aya ko?" Kallonta yayi sai yaga ita ma kallonshi take kallo mai nuna na fa sanka ba zaka iya ba, sunkuyar da kai kawai yayi yana murmushin jin dad'in yanda ta san shi sosai tare da fatan ina ma mahaifiyarshi ce ta mishi wannan fahimtar, fita sukayi inda ya kaita gidansu dan ta gaisa da yan uwanta. Kamar yanda ya fad'a kam ya cika alk'awari, ba tare daya fad'a mata ba kawai yace ta shirya, sai kawai ganin tayi sun d'auki hanyar garin, tunda ta ga haka ta fara murna tana jin dad'i sosai, da suka je saida ya wuni kafin ya juyo ya barota, murna a gurin Amna ba magana yau zata kwana tare da ummanta, ba ita kad'ai ba ita kanta tanti tayi farin ciki sosai, da dare da sukayi waya da Hamna ta fad'a mata gata nan ita kanta sai taji kamar tayi hira, anan take tambayarta me yasa yanzu ta b'oye lambarta in aka kirata sai dai ya nuna numéro unkwnon sannan me yasa bata Whastup? Haka kawai shine abinda ta fad'a mata, a wajensu Hamna ma da Ummy komai yana tafiyar musu daidai, sai dai basa cikin kwanciyar hankali, kullum Hamna tana fad'a ma Ummy idan fa asiri ya tonu tana jin tsoron abinda zai faru, ita ma kuma ta sani akwai gagarumar matsala, amma a ganinta lokaci ya k'ure musu. Tanti Hadiza ta ga abinda yafi k'arfinta, bata san yaushe kuma a wane lokaci Amna ta zama marar kunya ba, dan tunda ta zo idan yau bai zo ba gobe zai zo, a gabanta saita rumgume shi ko ta sumbace shi, idan suka shiga d'akinta duk da babu abinda ke shiga tsakaninsu, amma irin yanda yake jin dariyarsu da maganganu k'asa k'asa abin nasa kanta girma, idan kuma dare yayi suna waya wani abun idan ta fad'a saita kalleta da mamaki, shiyasa yanzu daya shigo gidan ita kuma saita shiga mak'ota ko kuma ta shige d'akin mijinta ita ma, a haka ta kammala sati d'ayan nan suka koma gida. Lieutenant ya fara mata k'orafi kan rashin dawowarta kan lokacin data fad'a mishi, amma sai take fad'a mishi basu gama bane ya k'ara hak'uri, har saida Hajia ta fara fad'a wanda Ummy tace kamar wak'a take jin fad'an nata, tunda dai har ta riga data tafi to anyi mai wuyar, a haka har lokaci ya k'ara kwararawa. *Bayan Wata Biyar* *France*: tunda ta shiga watan ta dama aka basu lokacin da za'a kawota kafin ta fara nak'uda, dan haka k'arfe *11: 54* suka shiga da ita d'akin haihuwa, Ummy bata san tana kuka ba saida wata banasariya ta dafa ta tace mata ta dinga mata addu'a zata haihu lafiya, tunaninta a lokacin shine idan fa aka samu matsala ya zatayi? Alwala ta d'auro ta shiga fad'awa Allah kukanta, bata matsa daga kan sallayar ba misalin *12:38* aka sanar da ita haihuwar Hamna lafiya, yaron bai dameta ba sai mahaifiyar da take tambayar ya take? Lafiya lau ita ma aka fad'a mata, saida tayi sujadar godiya ga ubangiji kafin ta shiga ganinta, murmushin daya sub'uce mata ne yasa Hamna dake kwance kallonta tace "Ummy lafiya?" Dake tsaye inda take kusan gadon jaririn ta sake dariya taja hancin yaron tace "Ya rantse saiya zo duniya, gashi dai ya zo yanzu kuma *BADAK'ALAR* zata fara musamman mahaukacin ubansa yasan dashi." Jim ta d'anyi saboda haushin Ammar data sake ji, har ga Allah tana b'oyewa ne dan kar Ummy taji ba dad'i, da k'yar ta kalleta tace "Kin fad'awa Abba ne?" Girgiza kai tayi tace "Hamna ba zan sanar dashi yanzu ba, kema kin sani ina fad'a masa zai biyo jirgi ya taho, ni kuma ina so mu fara tafiya gida na d'an shirya ki da kuma ni saina kira na fad'a musu." Shiru tayi kawai dan bacci ke son d'aukarta, saida aka k'ara tabbatar da lafiyarta da bebyn sannan aka sallamesu bayan an bata magungunan da zasu taimaka mata, suna zuwa gidan da suke Ummy ta zama mai haihuwar tare da anfani da duk abinda zai kawo mata ruwan nono wanda dama ta tanede shi saboda ranar, sai lokacin ta kira gidan ta sanar dasu, lieutenant yayi murna sosai da kuma fad'an rashin dawowa har haihuwa ta risketa tana nesa dasu, ya fad'a mata zasu zo tare da Hajia dan ba zai yarda ta taho yanzu ba, saita nuna masa ba komai kawai idan sukayi ko sati biyu zata dawo, tunda Zeituna ma gaf take da haihuwa bai kamata ya taho ya barota ba, da haka ya gamsu ya zauna sai hotunan yaro da suka game gidan da familyn cikin d'an lokaci. *Gaga's house* da dare suna tafiya a hankali a cikin unguwar ya ga duk tayi sanyi sosai ba yanda ya saba ganinta, jawota yayi jikinshi yace "Lafiya? Me kike tunani?" Saida ta d'ora hannunta kan k'irjinshi tana takawa a hankali tace "Hamna nake tunani, tunda na tashi yau nake tunaninta ina ji kamar wani abu na faruwa da ita, ta canza sosai amma kuma bata son yin doguwar magana da ni, bansan me yake damunta ba." Shafata yayi yace "Karki damu kinji, watak'ila bata jin dad'in zaman gidan nan ne shiyasa, amma idan kina so saina kaiki ki ganta amma fa bayan kin haihu." Murmushi tayi tace "Nagode." Wayarshi tayi k'ara yana dubawa ya ga kiran Amar, yana d'auka Amar tsabar farin ciki da kuma tsokana yace "Kai yaro kana ina? Ka zo gida fa Ummy ta haihu." Gabanshi kawai yaji ya fad'i ba tare da sanin dalili ba, amma saboda jaraba sai yace "Amar ni ne yaron? Ni ne dai yaro ko? To ka bari na dawo gidan zaka maimaita haka da bakinka." Amar ne yace "Naji dai, yanzu ka duba WhatsApp d'inka na tura maka hoton bebyn, anan dai gida kowa ya damemu da cewa wai yafi kama da kai, ni kuma a ganina ai dani da kai duk d'aya ne." Murmushi Ammar yayi yace "Hakane, amma ai na fika manyan ido, na fika dogon hanci, kai kawai gaskiya suka fad'a na fika kyau." Yana fad'a kuma ya kashe wayar ya shiga WhatsApp, dannawa yayi foton ya fara alamar bud'ewa, fad'uwar da gabansa ya sakeyi yasa shi d'auke idonshi daga kan yaron, a hankali ya sake kallonshi idonshi bud'e kamar ba yaron da aka haifa yau ba, sanye da kayan sanyi masu hula safar k'afa data hannu, hancinshi tubarkallah zungurere. A hankali yake jin abun na shigarshi kamar sihiri, ba zai iya tantancewa ba k'auna ce ko soyayya, amma dai k'anan nashi ya shiga ranshi daga kallo d'aya, murmushi yayi ya jawo Amna yace "Kinga Ummy ta haihu." Da sauri ta k'ura idonta tana fad'in "Na gani." Tana ganin yaron cikin farin ciki tace "Wow mai kama da jarumi na." Kallon idonshi tayi tace "Kamar kayi kaki ka tofar wallahi." Kallonta yayi, haka kawai yaji ya tsargu sai kawai ya share yace "Haka zaki haifo naki kema sak ni." Ko da suka dawo gida sun samu anata wannan murna, lokacin Zeituna ma ita kawai tasan me take ji ana dai ganinta, saida dare yayi ta fara nak'uda sosai, likitar su Ammar aka kaita da gaggawa, ta jima tana nak'uda ta galabaita sosai, ana kiran sallah asuba ta haifo jaririyarta ita ma mai kama da ita gashi har saman goshinta luf luf, amma ana buk'atar k'ara mata jini dan ta rasa shi, lieutenant ne yace a duba nashi, har an duba za'a d'iba Ammar yace a d'ibi na shi, lieutenant yace "Ai akwai buk'atar a fara dubawa idan yayi daidai." Murmushi ya masa yace "Ni fa jininka ne, ina da masaniya akan jininka da nawa Abba, amma in baka yarda a dararawa matarka ba sai an duba ni to a duba." Dariya kawai lieutenant yayi, duk da haka da aka shiga ciki saida yasa aka gwada jinin sannan aka diba aka saka mata, tubarkallah masha Allah, a cikin kwana d'aya an samu k'aruwar yara biyu *Fatima Zahra* da kuma *Shureim*, fatan Allah ya raya. *Bayan sati biyu*... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _47_ *Bayan sati biyu* yau Junaid ya tafi makaranta yana cikin koyarwa aka ce ana sallama da shi, yana fitowa yayi mamaki sosai ganin *Sani* tare da *Salma* a tare dashi, k'arasawa yayi suka gaisa ita ma ta gaishe shi, da mamaki yace "Tonton lafiya dai ko?" Saida ya kalli Salma ya mata alamar ta basu wuri kafin ya gyara tsayuwa yace "Lafiya ba lafiya ba Junaid, wata alfarma na zo nema a wajenka." _*Anzo wajen, Sani dai d'an Innusa ne yayan Alhaji, wanda yace baya buk'atar taimako ko alfarmar Alhaji Suley, dalilinshi yasa Hajia dagewa ta ga yaranta sun zama masu muk'ami a gwamnatacce, meya faru yau da har aka zo neman alfarma a wajen ahalin Suley?*_ Junaid ne yace "Tonton wace irin alfarma kuma? Ai daka kirani a waya sai naje har gidan ma." Murmushin jin dad'i yayi yace "A'a ba sai ta kai ga haka ba, dama akan maganar makarantar yer uwarka Salma ne?" Saida ya kalli inda take tsaye da uniforme d'inta yace "Wani abu ne ya faru?" Cike da damuwa yace "Kasan dai yaran yanzu ka haifesu ne baka haifi hali ba, tana tare da k'awaye ne da basa jin magana wanda yasa sukayi rashin kunya wa malaminsu, hakan yasa aka koresu tare da tab'a musu conduite (bansan me zan kirashi da turanci ba), yanzu tsawon sati d'aya kenan muna ta bibiya da bayar da hak'uri dan a gyara ta koma, amma abun ya ci tura wallahi, shine sai jiya malamin yace idan akwai wani babba ko malamin da muka sani mu mishi magana, shiyasa na tuntub'e ka dan kasa baki dan Allah ta koma." Ajiyar zuciya ya sauke, zai so ya taimaka musu sai dai kuma yaji Hajia tace duk wanda d'aya daga cikin iyalin Innusa ya neme shi taimako ya fara fad'a mata kafin yayi, bai nuna masa komai ba sai cewa da yayi ba komai zaiji da matsalar, godiya ya masa suka koma suka tafi, shi ma aji ya koma da tunanin yanda zaiyi, shin ya fara fad'a mata ne ko kuma kawai yayi? Da wannan tunanin ya kammala ya dawo gida, da rana tsaka ya tarar da tashin hankalin da baiyi tsammani ba. Yaran gidan na wasa tare da Huda wacce ita kanta bata cika sakewa ba idan tana cikin yaran, Hajia na fitowa ta gansu sai kawai ta musu tsawa tace "Kai, maza ku wuce ciki, karna sake ganinku da yarinyar nan dan matsatinku da nata ba d'aya bane, kuji ni ko." Kai suka d'aga mata alamar eh suka shiga ciki, wannan magana data fad'a a kunnen Maryama wacce ita ma ta fito kiran Huda dan bata so tana shiga cikinsu, tana jin haka ta matso tace "Da me suka fita Hajia? Kina babba kike fad'in maganar nan a gaban yara, ina ce dai nan daga jikokinki sai jikokin Hajiarsu Jibril, ko ita ma jikokinta basa da damar yin wasa a gidan nan ne?" Su Zeinabu dake zaune suna gyara kayan da zasuyi girkin dare dashi ne suka kalleta, Husseina ma dake gefensu tana b'are musu tafarnuwa ce ta kalleta, Hajia ce tace "Suna da dama, amma dai banda wannan 'yar taki." Wani kallo ta mata tace "Saboda me? Saboda ita ba jikarta bace? Na ga ita ma daga tsatsonta ta fito, dan haka ki barta ta wala a gidan ubanta." Ta k'arashe cikin d'aga murya. Mik'ewa Husseina tayi ta matso kusanta da mamaki tana kallonta tace "Me kike nufi Maryama? Tsatsona daga ina?" Cikin d'aga murya tace "Eh tsatsonki, ki tambayi Jibril zai fad'a miki yanda akayi haka ta faru." Kallon Hajia tayi tace "Ba kina ganin karuwa ce ni ba, to d'an gidan nan ne ya mayar dani karuwa, shi ya bani lasisin zama abinda na zama, dan haka shima yana da kamashon duk abinda na aikata, nima da fari 'ya ce kamar kowa, Jibril ne ya tirsasni har na samu yar da ban haifeta a gidan aure ba." Hajia data kafeta da ido sai kawai ta tintsire da dariya har da d'an rik'e ciki, kallonta kowa keyi da mamakin abinda take ma dariyar, Husseina kuma k'asa tayi da kanta dan tasan ita take ma dariyar sai Inna lillahi da take maimaitawa, Soueiba taso tashi tsaye amma jikinta taji yana rawa rawa sai kawai ta damk'e kujerar da take zaune tana kalmar shahada, a hankali ta kai idonta kan Huda a lokacin ita ma tana kallonta saboda jin tana kalmar shahada, ido cikin ido suka kalli juna ita da yarinyar, ba za tace tana k'in yarinyar ba, sai dai tunaninta ya akayi Jibril ya musu haka. Hajia dake dariyar nan ce ta kalli Husseina tace "Kin gani, illar karuwanci kenan, ke kinyi gashi kuma har yanzu bai daina bibiyarku ba, kin haifeshi a yawon dandi, yayi k'ok'ari shi ya haifi nashi yaran a aure, amma gashi jikanki ya kawo miki yar dakan kuka." Cike da shak'iyanci ta sunkuya tace "Ina miki barka da k'ara samun k'aruwa." Wata dariyar ta kece da ita ta juya zata tafi sai kuma ta kalli Maryama tace "Ni ban ma yara da jikokina irin wannan tarbiyyar ba, in dai har kinga d'an gaba da fatiha a ahalin nan to ki tabbatar daga wani k'ugun ya fito amma ba tsatson Zeeya'atu ba, can ku k'arata da matsalarku." Tana fad'a ta juya ta bar wurin, Maryama ma ta kama hannun Huda zasu juya ta ga Junaid, kallon kallo akayi inda yake binta da wani kallo mai wuyar fassarawa, girgiza kai yayi yace "Ban tab'a kawo haka ba Maryama, zuciya d'aya nake sonki kuma nake zaune dake, ashe Huda yar d'an uwana ce baki tab'a fad'a min ba? Nagode da abinda kika min, amma a gaskiya aurenki ya fice a raina, sam ba zan iya ci gaba da zama dake ba, kawai kije na sakeki." Tab'e baki tayi tace "Nima ban nemi takardata a wajenka bane dan karka tambayeni dalili, amma ka sani auren gidanka ya jima da fice min a rai, shiyasa ban bari ma na samu ciki da kai ba bare na haihu, hakan zaisa iyaye su dinga tausata da cewa nayi zaman 'ya' ya, ni kuma bana d'aya daga cikin matan da bak'in cikin namiji zai kashe su." Tana gama fad'a ta kama hannun Huda suka nufi inda Soueiba ke zaune, tura mata ita tayi gabanta tace "Zan koma gidan iyayena nima, nan kuma gidan ubanta ne ta zauna tare da ku, ruwanku ne ku bata guba ta ci ko ku taushe mata kai da matashi har ta daina numfashi, ni dai na sadata daku na huta da bata amsar cewa zai kaita wajen yan uwanta ita ma." Juyawa tayi ta koma b'angarenta, cikin sauri da kuka da bata san ko na miye ba ta had'a kayanta ta bar gidan ko Huda bata san fitar ta, Zeinabu da surutu ke ciciyarta kai tsaye b'angaren Jamila ta nufa wacce a lokacin ke jin ciwon baya shiyasa ko gaishesu bata zo ba yau, tana shiga ta same ta zaune k'asan carpet ta mik'e k'afafu, ba tsayawa ko tunanin wani abu kawai daga tsaye tana kallonta tace "Ke Jamila, ashe Jibril d'an iska ne shima shiyasa Hajia ta had'aki da shi, yanzu gashi nan asiri ya tonu wannan yarinyar Huda 'yar shi ce." Kamar ta k'ara sara mata guduma a tsakar baya, sai kawai tayi wani zullo kamar an fizgota tare da dafe baya ta kwamtsa salati ido rufe ruf, hannu ta fara yarfawa tana fad'in "Inna lillahi wa'innailaihi raju'un, la'ilaha illalah, Mama bayana, wayyo Allahana Mama, bayana Mama zan mutu, wayyo Mama..." A rikice ta fita ta nemo taimako, Soueiba ce tayi k'arfin halin kiran Jibril ya zo a matuk'ar gigice, ganin halin data shiga jikinta sai rawa yake yasa shi lailayarta a hannu ya nufi mota da ita, a baya suka biyoshi da kayan haihuwarta aka nufi likita, Ammar na asibiti a lokacin aka kawota, ko da aka shiga da ita aka ga jininta ya hau ga kuma borin gishiri ta yanda ba zata iya haihuwa da kanta ba yasa docteur d'in cewa kawai a mata aiki, Jibril na kuka yace Ammar dan Allah yasa a dubata ta haihu ba sai an fasata ba, kwantar mishi da hankali yayi tare da umartarshi yasa hannu, yana saka hannu docteur d'in ya shiga d'akin tiyata (tun kafin a bud'a mère et enfants), cikin hukuncin ubangiji saiga santalelen yaro an fito mata dashi sak ubanshi, amma fa uta saida akayi da k'yar aka ceto ta kafin aka shiga bata kulawa, d'akin sama aka kaita tare da hana kowa shiga dan ta huta, a lokacin Jibril da Soueiba suna k'asa ne ta kalleshi da yanayin ka ban mamaki tace "Jibril ashe yaudararmu kake yi, ban tab'a tunanin haka daga gareka ba wallahi, sai ga yarinyar 'yar shekara bakwai wai a matsayin 'yarka." Jim yayi kanshi k'asa cike da kunya, ya jima haka kafin yace "Kiyi hak'uri Mama, tsautsayi ne da shar..." Da sauri tace "Sharrin shaid'an ko? Nasan abinda zaka fad'a kenan, wai duk uban daya tsula tsiyarshi a k'arshe sai yace maka sharrin shaid'an, kai yanzu kasan kammaninshi ne?" Jin yayi shiru yasa tace "Shikenan, yanzu ai ba fad'a zamu maka ba tunda na banza ne, kawai saimu rumgumi k'addarar a yanda ta zo mana." Cike da son nad'e tabarmar kunyarshi yace "Ko akwai abinda ake buk'ata yanzu?" Cikin sanyi tace "Akwai mana." Zana mishi tayi duk abinda buk'ata ya tafi zuciyarshi a cunkushe babu dad'i, saida ya kawo komai da ake buk'ata har lokacin Jamila na d'akin hutu ita kad'ai ya juya ya koma, bai zame ko ina ba sai gidan malam Rabi'u, fitowa yayi a soron gidan suka zauna kan tabarma, cikin mutumci suka gaisa kafin Jibril yace "Malam nine mahaifin Huda, maganar gaskiya sanda abinda ya faru har ya faru bansan yer uwata bace, saida nasan waye kakana saina tabbatar da cewa ashe *dara ce ta ci gida*." Kallonshi yayi da mamaki, Huda yar shi ce dama? Nunfasawa yayi yace "Ikon Allah, 'yarka ce dama? To ya zaayi sai hak'uri ai komai ya wuce, nima waccen d'in daya faru ina mai hak'uri ku yafe min, wallahi daga abinda ya faru yanzu nayi nadama." Kallonshi kawai yayi bai tanka ba, malam d'in ne yace "Mahaifinka har yanzu bai zo ya ganni ba, nasan shima hushi yake dani kamar Husseina." Kallonshi yayi yace "Hajia kam tana hushi da kai, amma Abba zai iya zuwa idan kana buk'atar hakan." Kallonshi yayi yace "Idan ka min haka zan ji dad'i sosai." Jinjina kai yayi yace "Ba komai zai zo." Mik'ewa yayi yace "Ni zan koma, da yake matata ta haihu yau d'in nan." Da fara'a sosai yace "Ah masha Allah, me aka samu?" "D'a ne, aiki ne aka mata." Tsaye ya mik'e shima yace "Allah sarki, Allah bata lafiya ya raya kan sunna, yanzu ku nawa ne ga Labaran?" Murmushin yak'e ya masa yace "Mu biyar ne, maza uku mata biyu." Ammar na zuwa gida ya samu Junaid zai shiga falon Hajia, gaisawa sukayi sai Junaid yace "Yawwa dan Allah muje tare ka rakani wajen Hajia." "Lafiya?" Ya tambaya fuska a had'e, nan ya kora mishi bayanin abinda ya faru, kallonshi yayi yace "Yanzu kana nufin baka taimaka ba saika nemi izininta?" "Ni ba izininta zan nema ba, zan dai fad'a mata ne kamar yanda ta buk'ata." Girgiza kai yayi yace "Shashashu ta d'aukeku, wallahi na tabbata dan tayi gadara da an nemi alfarma ne a wajen zuri'arta shiyasa tayi haka, ko ka manta abinda Alhaji ya fad'a mana ne wanda yasa shine silar da bata shiga sabgar data shafi Alhaji Innusa da iyalinshi, dan haka kawai kaje ka taimaka musu indai zaka iya yan uwanka ne." Cikin fargaba yace "To ai ina jin tsoron abinda zata iya yi kuma idan taji, ka fa san halinta." Tsaki Ammar yayi ya shak'o bakin aljihun rigarshi ya fizge shi har zuwa motarshi ya bud'a ya jefashi ciki, zagayawa yayi ya shiga shima suka tayar, suna barin gidan yace "Allah ya baka dama amma ka kasa anfani da ita wai har saika nemi izinin wata hallita, wannan wace irin rayuwa ce kuke? Matar da ko dukanku ba zata iya ba tsabar k'arfinta ya k'are, yo ni duk hukuncin da zata yanke ko take yankewa a kaina ai alkairi yake zamar min, dan haka ta dad'e bata yanke hukuncin ba." Bai tsaya ko ina ba sai cikin harabar makarantar, tare suka fito inda Junaid ke gaba har ofishin shugaban makarantar, bayan gaisuwa suka fad'i abinda ya kawosu, sosai suka bada baki tare da alk'awarin jan kunnenta hakan ba zai sake faruwa ba, nan komai ya wuce suka dawo bayan enveloppe d'in da Ammar ya aje mishi a matsayin ya sha ruwa, daga nan tare suka wuce d'an gulbi suka sanar dasu yanda ake ciki, farin ciki da murna basu misaltuwa wajensu. *Tazarar* minti sha biyar ta saka tsakanin lokacin saukar jirginsu da lokacin data fad'a mishi ya zo d'aukarsu, a wannan tsakanin ne sanda jirginsu ya sauka ta samu ta tura Hamna gida, lokacin na cika kuwa sai ga lieutenant tare da dreba suka d'auketa, tunda ya karb'i Shureim ya kasa saki sai wasa yake mishi kai kace yana fahimtarshi, gidan Gambo suka sauka anan suka samu tarba ta musamman kamar wasu sarakai, sun ci sun sha Alhamdulillah kuma kwanansu d'aya, washe gari da safe kuma suka shirya dan jirginsu zai tashi lieutenant yace ba za ayi tafiyar mota da yaronshi ba *(Shureim Ammar)*, Hamna kad'ai ta rakasu filin jirgi, a lokacin da suka juya zasu shiga jirgi sai taji kamar Ummy na tafiya da zuciyarta, bugawar zuciyarta ce taji ya k'aru, bakinta sai rawa yake zuciyarta na karkarwa a tsakanin k'irjinta, suna daf da shiga Ummy ta juyo ta kalleta, idonta kad'ai suka ankarar da ita halin data shiga ganin za ayi mata nisa da abinda ta haifa, dawowa Ummy tayi ta tsaya gabanta ta mik'a mata shi, jiki na rawa ta karb'eshi ta sumbaci ko ina na fuskarshi, k'ura mishi ido tayi tana kallo wanda hakan yayi sanadiyar zubar hawayenta akan jikinshi, Ummy na gani tace "Hamna kuka kike?" Kallon Ummy tayi tace "A'a." Mik'a mata shi tayi ta share hawayenta, cike da tausayinta Ummy tace "Hamna zan kula miki da shi kamar yanda ke ma zaki kula dashi, ki ci gaba da addu'a insha Allahu komai zai daidaita, ni zan d'auki alhakin duk abinda zai faru, ki kula da kanki kinji ko? Sannan kar kiyi wasa da shan magunanki akan lokaci saboda zasu taimaka miki sosai." Kai kawai ta jinjina alamar to, tana kallo suka shiga sannan ne dreban da suka zo tare ya fara mata oda, juyawa tayi ita ma suka koma gida sai kuka take. Su Ummy kuma suna zuwa gida suma akayita farin cikin ganinsu, inda kowa ke karb'an beby yana gani. Har d'aki suka sameta tare da Amna suka gaisheta, zaune sukayi inda Ammar ya k'arasa gaban gadon ya sunkuya ya d'auke shi, a hankali yayi zaune yana kallon fuskarshi, kowane motsi nashi yana binshi da hankali da nutsuwa, shi kam har ga Allah abu na daban yake ji akan k'ananshi da bai tab'a jinshi akan kowace hallita a doron duniya ba, cikin nutsuwa ya rab'ashi a jikinshi ya rumgume sosai ya d'ora bakinshi kan wuyanshi, lumshe ido yayi sakamakon tattausan turarenshi daya shak'i k'amshinshi, bud'a ido yayi ya kai bakinshi kan labb'an shi da nufin sumbata, sai kawai yaron ya bud'a baki ya d'auka nono ne za'a saka masa, caraf ya karb'e leb'enshi na k'asa ya shiga tsutsa da sauri sauri, baisan sanda dariya ta kubce mishi ba saiya shiga k'yak'yatawa ba tare daya cire mishi leb'en ba, Amna na kallonsu sai taji ina ma nasu yaron ne a hannunshi, Ummy na ankarewa da haka ta taro mishi hannaye tace "Kawo shi yasha." Da k'yar ya cire leb'enshi daga bakinshi ya mik'a mata shi. *Kwana uku* Duk abin duniya ya shawa Hamna kai, sam yanzu ta daina jurar wulak'ancin Aissata, zuciyarta kawai tafasa take ita kanta bata san dalilin b'acin ran nata ba, yau ma hakane ya kasance da safe ta mata duk abinda takeyi, amma tsabar fitina sai Aissata tace ta gyara mata d'aki, ta shiga tana gyara ta shigo tana mata kinibibi, ganin tayi banza da ita tana aikinta yasa Aissata cewa "Kinga wurin nan bai fita ba." A k'ufule ta kalleta tace "Saiki gyara da kanki mana." Cikin d'aga murya tace "Hamna ni kike fad'awa haka? kin rainani ko?" "An rainakin kiyi abinda zakiyi." Mik'ewa tayi ta kalleta sosai tace "Ke nafa gaji da abinda kike min, tun farko Allah ya isar mahaifina ce ta min katanga da dakuwa dake, amma wallahi badan haka ba ke baki isa ki min abinda kika min ba." Fad'a Aissata ta fara yi da hausa da zarma da french saboda harshenta bai nuna ba, jefar da abun gugar tayi ta harareta sama da k'asa tace "Matsalarki ce." Fita tayi daga d'akin ta shiga nata, bata tsaya komai ba ta had'a kayanta tsaf a akwati ta fito, dreba ta samu tace ya ciro mata ticket, shima bai b'ata lokaci ba ya ciro ya kawo mata ta ajiye. Tunda asuba ko da tayi sallah ta shirya, *07:30* ta fito ta samu dreba yasa jakarta suka bar gidan, Gambo bai sani ba haka ma Aissata dake wurin motsa jikinta da babu wata tsiya da take ragewa. Suna zuwa ta shiga bus suka d'aga zuwa Maradi, ita kanta tasan saboda wannan d'ayan ne zata koma garin nan, wannan d'ayan kuma ba kowa bane sai *Shureim Ammar Hassan Suley Gaga*. *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.N.A]* ☆🖊️ _Bismillahir rahamanir rahim_ _48_ Tana shigowa gidan ma yer uwarta ce ta fara karo da ita tana d'an safa da marwaa tsakiyar gidan, suna had'a ido dukansu ihu suka saka Hamna ta saki jakarta suka rumgume juna, cikin farin ciki Amna dake tura tulun ciki tace "Ya kika zo mana haka ba zata? Ke da wa kika zo?" Bata amsa tambayarta ko d'aya ba ta saketa tana k'are mata kallo tace "Amna dama haka kika koma? Yanzu kenan da ban zo ba da sai dai naji labarin haihuwarki?" Hararanta tayi tana d'an kai mata duka a kafad'a tace "Haihuwata ko haihuwarki dai." "Me?" Ta fad'a da k'arfin bala'i, ba iya gabanta bane kawai ya fad'i har jinin jikinta ma saida ya matuk'ar hawa, dariya ta mata tace "Idan Amna ta haihu ai Hamna ce ta haihu." Ajiyar zuciya ta sauke tace "Wai Allah, amma dai cikin nan naki yan biyu ne ko? Wannan abu haka." Cikin shagwab'a tace "Shiyasa na so nayi éco (scanning) amma yah Ammar yace sam bai yarda ba, yanzu haka gobe zan koma awo har na cinye sati biyun da aka bani, nak'udar tsaye kawai nake fama da ita." "Karki damu, ai da sati biyu biyu ma kina iya cinye wata biyu, kawai ke dai karki zama lusara mai son jiki, ki dinga tafiya mai tsayi saboda ko nak'uda ta taso miki ma zata zo miki da sauk'i, amma kin fara zubar da ruwan zak'i?" Waro ido Amna tayi a hankali sai kuma ta k'ank'ance su tana kallonta da mamaki, ba tare data daina mamakin ba tace "A ina kika san haka ke kuma sai kace wacce ta tab'a haihuwa?" Tsuru Hamna ta mata da ido, saida ta k'ak'alo abinda zata fad'a kafin tace "Kiji sai kace ba mace ba, to wannan ne sai mace ta haihu zata sani." Jakarta ta d'auka suka nufi falon Hajia tana fad'in "Muje ki gaishesu sai muje b'angarenmu musha hira." Sallamarsu tasa wanda ke falon suka kallesu, yan biyu ne dai gasu amma duk sun canza, Hamna ta k'ara haske kan wanda take da a farko, jikin nan nata duk da tana shan wahala a wurin Aissata amma ya kwanta luf dashi, Amna kuma ta k'ara duhu sai kuma cikin yasa tayi muni ba kamar kafin ta d'auki cikin ba tsaf da ita, ana gaisawa ana mamakin tahowarta katsam haka babu sanarwa, Ummy na d'aki take jin kamar maganarta, tana lek'owa ta ga dai ita ce da gaske, saida suka gaisa da kowa sannan ta wuce d'akin Hajia dan tun sallah la'asar bata fito ba jikin ya d'an k'ara nauyi sosai bata san dai nunawa ne, kamar mai sand'a ta shiga tana sallama har ta zaune kusanta a k'asa ba tare data yarda sun had'a ido ba, bata amsa sallamarta ba bare gaisuwarta tana mamakin dawowarta bada izininta ba. Cikin wani irin amon murya tace "Meya dawo dake? Waya baki izinin dawowa ba tare dana amince ba? Ke ce kika zab'i dawowa ko kuma shi Gambon ne yace ki dawo?" Cikin sanyin murya tace "Gaskiya Hajia basu san da fitowa ta ba, kawai na gaji da zaman can ne saboda tanti Aissata ta mayar dani kamar wata baiwarta, kuma Abba ma har Allah ya isa ya min idan na b'ata mata rai, jiya ma mun samu sab'ani ne shiyasa na tahowa ta dan nasan Abba na iya dukana idan ta fad'a masa na mata rashin kunya." Kallonta Hajia tayi ta mik'e tsaye cikin b'acin rai ta gaura mata mari a fuska, dafe kunci tayi da sauri ta k'ara sunkuyar da kai, cikin masifa tace "Hamna kinsan dalilin da yasa na turaki can? To saboda ina so nasan abinda ke faruwa acan d'in ne, ina so naga abinda yasa bata so kowa ya rab'eshi sai ita kad'ai, amma da yake mahaukaciya ce ke shine kika dawo min haka ko? To tashi ki bani wuri, ni kuma zanje da kaina nayi aikin dan ba zan haifi d'a a cikina ba kuma wata ta fini cin moriyarshi ba." Fita tayi ita kuma ta shiga masifa tana fad'a, tana fita d'akin Ummy ta shiga, tana ganinta bata tsaya komai ba tace "Hamna meya dawo dake? Ya akayi kika zo baki sanar min ba?" Marairaicewa tayi tace "Ummy wallahi Tanti Aissata ta addabeni, kawai ta b'ata min rai ne jiya shiyasa na baro mata gidan." "Amma me Hajia tace miki da kika taho ba da umarninta ba?" Tab'e baki tayi tace "Tana can tana masifa mana, wai zata je da kanta Niamey d'in ta ga wace irin rayuwa suke, wallahi da za taji tawa da sai nace karta tafi, dan matar nan da gangan ma zata iya d'ora mata hawan jini." Murmushi tayi tace "Hamna ince dai ba yaron nan yasa kika dawo ba ko?" "A'a Ummy, kawai na dawo ne." Ta fad'a idonta akan Shureim dake bacci, fitowa tayi ta d'auki jakarta ta kai d'akinsu, saida tayi sallah magriba tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar kanti da d'an kwalinta sannan ta fito, Farisa tasa ta gyara mata d'akinta ita kuma ta sauko k'asa, saida ta shiga ta ga Zeituna da Fatima masha Allah yarinyar kamar ka fizge a hannunta ga uban gashi, suna gaisawa ta fito ta nufi wajensu Umaimah. Mamaki ne ya kusa kasheta data shiga d'akin, yarinya 'yar k'walisa uwar kwalliya da tsabta, amma wai ita ce zaune k'asa da d'aurin k'irji tana cin 'ya'yan tsamiya tana tofar da yawu, kan nan nata yayi daud'a ya tsufa abun ba kyan gani, daga tsaye take k'are mata kallo tana mamaki, tafin k'afarta abinka ga farar fara yayi duhu, a take a wurin taji Umaimah ta fita a ranta, dan duk yanda kake ji dai zaka daure ka gyara jikinka tunda har kana iya cin abu kuma kana taka k'asa, ko baka gyara dan komai ba ka gyara dan kar namiji ya ga makusarka. Daga nan tsaye suka gaisa ta wuce b'angaren yer uwarta, ba wai son kai ba ko dan tana yer uwarta, amma tana dosa b'angaren ma k'amshin turaren tsintsiya ne ya mata maraba. Tana shiga ita ma zaune take k'asa ta mik'e k'afafu da suka kumbura sumtum, cikinta yafi na Umaimah girma nesa ba kusa ba, cikin nutsuwa take cin bredinta mai yanka nan tana shafeshi da la vache qui rit, zaune tayi ta fizge bredin tana fad'in "Sakarya kawai, kina da ciki kina ta fama da abubuwan da zasu bud'a miki yaronki a cikin cikin, ki zo kisha wahala kafin ki haihu." Hannu ta tara mata tace "Taimaka ban wannan na k'arasa to." "An k'i." Ta fad'a tana d'auke d'an kwalin ta aje bayanta ta kalleta tace "Jamila wace asibiti take?" Cike da shak'iyanci ta wani murgud'a mata baki tace "Asibitin mijina mana." Sai kawai taji gabanta ya fad'i daga anbaton mijinta, da mamaki ta kalleta tace "Anya kuwa Amna bai koya miki iskanci ba, ke ma fa kin lalace yanzu." "A'a ni bai koya min ba, kawai dai abun ne kamar a karatu, yana biya min ni kuma na hardace shi a kaina." Tab'e baki tayi tace "Lallai mai miji." Amna ce tace "Yer uwa dama ina so ki zo, akwai matsala fa..." Duk da ta kai k'arshen abinda take son fad'a amma saida ta juya ta kalli k'ofar da taji sallamarshi. Yana shigowa ya tsaya kamar wanda aka dakatar dashi, idonshi cikin nata wacce k'afafunta ke tank'washe tana jujjuya wayarta dake hannunta, *sanyin idaniya*, yau ne ya tabbatar da kalmar sanyin idaniya da ake fad'a, domin kuwa sanyin nan bai tsaya iya idonsa ba saida ya zarce har k'ark'ashin zuciyarsa ya isar da sak'on cewa wata mai matuk'ar mahimmanci ta iso wacce akayi kewarta na wani lokaci, dawowa yayi hayyacinshi ya fara takowa yana sauke jakarshi daga kafad'a ya kalli Amna yana fad'in "Duniyata bak'uwa kikayi?" Kallon Hamna tayi tana dariya tare da bata gefen fumcinta da taga ya nufota tasan me zaiyi, sumbatarta yayi tana cewa "Sannu da zuwa, ya aiki, kayi hak'uri nayi nauyi ba zan iya tashi tarbanka ba." Jakar ya aje kan kujera ya zauna daf da Amna yana rik'ota jikinshi yace "Je sais ma chérie, ya kika wuni?" Cikin shagwab'a tace "Lafiya lau, kai fa?" Hamna ya kalla wacce a taswirar zaman nasu suna kusan juna ne dukansu inda shi da ita suke fuskantar juna Amna ce kawai ta shiga tsakaninsu, yana kallon ita kuma tana dalla masa harara, wani bala'in haushinshi taji saika mata yake, yanda har taji ya fara tasiri wajen jin haushin yer uwarta ma data biye masa, akan me zasu raina mata wayo haka? Dan ita bata da auren ko me? D'auke idonta tayi daga kansu sai Ammar ne da yace "Ke baki iya gaishe da mutane ba?" "Eh." Shine ta fad'a tana juya baki kamar zata tsinka shi, d'agowa yayi daga kishingid'en da yayi yana fad'in "Ke kankana ni? Ni kike ce ma eh?" Da sauri taja baya tana fad'in "An fad'a d'in, kaga malam karka takura min fa, na fad'a maka ka daina shiga harkata, ba wajenka na zo ba ni wajen yer uwata na zo." Jujjuyawa ya farayi alamar yana neman abunda zai jefa mata, da sauri ta tashi tsaye ta zagaya bayan kujera ta tsaya tana hararanshi, tsayawa yayi daga neman abun ya k'ura mata ido, a ranshi yace "Shegiya har tayi shirin gudu, ass kawai take jira." Mamakin k'ibar da yaga ta k'ara yake yi, saida ya k'ara kallo da kyau yace "Ke kankana, murguzawa, yaushe kika mulmuje haka? Me tonton ya dinga baki acan kika koma haka?" Cikin jin haushi tace "Tubarkallah maye ka ci kanka, ina ruwanka da k'ibata inba sa ido ba, to kurwata tafi k'arfinka maye kawai." Zunbur ya mik'e ya nufeta, tana ganin haka ta tattare rigar bi ta bayan kujerar shi kuma tsalle yayi ya dira bayan kujerar da niyyar tarbanta, cikin sa'a ta zille ta fita da gudu tana fad'in "Jarababbe kawai ka shafa min lafiya mana in kana da zuciya." Tsaye yayi ya dafe k'ugu da hannu d'aya yana binta da murmushi, wani dad'i yaji na ziyartarshi saboda yayi abinda ya jima baiyi ba, juyowa yayi kan Amna dake binsu da dariya kawai tana kallo, ita kanta tayi kewar wani abu data jima ba tayi ba, kallon dramarsu ba, dawowa yayi ya zauna yana sauke numfashi alamar gajiya. *01:39* ta farka saboda jin kukan Shureim, tasowa tayi daga kan gadon sanye da gajerar rigar bacci, a hankali ta bud'a d'akin ta lek'o tana hangen d'akinsu Ummy, akan abun matakala ta tangale hannu d'aya ta buga tagumi, sannu sannu wani tausayin yaron taji yana shigarta, *uwa* bata tare dashi, *uba* ma haka baisan dashi ba, ta jima tsaye tana tunani da taji yayi shiru kuma ta sake jin kukanshi, kafin daga bisani ta koma d'aki ta kwanta tana jin sautin har yau. Tunda ta dawo hayyacinta abun ya tsaya mata a rai, Huda 'yar shi ce dama, lallai ita kam kam ta gama auren Jibril kenan har abada, daga gadon asibitin nan gidansu zata wuce wajen iyayenta, kuma tayi niyya ko kasheta Hajia zatayi ba zata zauna dashi ba, bare ma tasan yanda Hajia bata k'aunarsu ba zata matsa mata ba, tana wannan tunanin ya shigo d'akin da sallama tare da wasu abokanshi su biyu, su Soueiba da Zeinabu suka amsa suka gaisa sosai, zaune yayi bakin gadon yana kallonta ita ma zaune take k'afafu mik'e sai rigarta data d'an d'age kad'an, cikin kulawa yace "Ya jikin naki?" Kallon da take masa yasa ya fara tsarguwa da shi, saida tayi niyya sannan tace "Jiki ba sauk'i." Kowa na d'akin kallonta sukayi inda Zeinabu tace "Jamila ba'a cewa haka, da sauk'i ake cewa duk tsananin da ake ji, ko kuma kice angode Allah." Kallonta tayi a harzuk'e ta nuna shi da yatsa ta d'ago daga zaman da tayi tace "Bayan duk abinda ya min ne zai wani tambayeni ya jikina? Jibril akan me zaka k'i fad'a min gaskiya? Kana ji kana gani 'yar iskar nan ta dinga min buru-uba a cikin gida tana nuna min ta ma fini saninka, ashe gaskiya ta fad'a nice mahaukaciya da..." Soueiba ce tace "Jamila dan Allah kiyi shiru ki k'yaleshi, d'inki aka miki fa karki tada shi da d'aga muryar nan da kike, ko tari ba so ake kiyi ba bare wannan fad'an haka." Kallonta tayi cikin zubo da hawaye tace "Amma duk abinda ya faru ai shi ya ja, ni yau bak'in ciki na yana ta hidima da yarinyar nan amma saiya nuna min kawai yana yi ne dan ya ma yah Junaid kara, sannan gabanshi babu irin iskancin..." Jibril ne yace "Naji na d'auka Jamila kiyi min duk abinda zakiyi, amma dan Allah yanzu kiyi shiru ko dan halin da kike ciki." Tank'washe k'afafunta tayi ta kifa kanta tsakanin cinyoyinta ta fashe da kuka, da sauri Soueiba da Zeinabu suka tashi suna bata hak'uri Zeinabu na k'ok'arin d'agata tana fad'in "Ki gyara zamanki mana karki ji wa kanki ciwo a banza." Tasowa yayi ya tsaya gabanta ya sunkuya ya ja k'afafunta ya mik'ar mata dasu, hannayenta ya b'amb'are ya tallabo fuskarta yana kallon idonta yace "Dan girman Allah Jamila karki cutar da kanki akan banza irina, ki kwantar da hankalinki ki nutsu, ki kula da kanki da yaronki kinji, ba dan ni ba kiyi dan iyayenmu." Fizge fuskarta tayi ta kawar da kai gefe, ganin ta daina kukan yasa shi zagayawa ya kalli abokanshi dake rik'e da bebyn, fita sukayi inda Zeinabu da Soueiba sukayi ta bata baki kan karta yarda damuwar ta kusa illata ta. *Safiya* na yi ta gama shiryawa dan zuwa ganin Jamila, dama tare suka shirya tafiya dan haka suka fito duk a tare, Hamna na tare da Ummy wacce yau zata fara zuwa aiki, tayi fes da ita kamar tayi bik'i fa haka ma Shureim yasha shiri tsaf da shi, saida Ummy ta bud'a mota ta zauna cikin mota suka k'araso wurin, da girmamawa dukansu suka ce "Ina kwana Ummy." Kallon Amna tayi tace "Lafiya lau, antashi lafiya?" "Lafiya lau." Amna ta amsa, matsowa Ammar yayi kusan Hamna dake rik'e da Shureim ya tara hannayenshi zai karb'eshi, kallonshi tayi da fararen idonta haka kawai ta tsinci kanta cikin jin dad'i yanayi, mahaifin d'anta zai karb'eshi a hannunta, murmushi tayi da ita kanta bata san ya zo mata ba, zata bashi shi cikin had'e fuska Ummy tace "Kawoshi na kusa makara." Take murmushin fuskarta ya b'ace ta sake kallonshi, wallahi bata san wane irin yanayi ne take ji ba a game dashi, amma dai har k'asan zuciyarta tausayi taji ya bata da Ummy ta k'i yarda ya amshe shi, mik'a mata shi tayi suna kallo ta rufe motar ta tayar ta bar gidan. Amna ya kalla ya kama hannunta yace "Muje." Suna gaba Hamna na bayansu har suka shiga gaba ita baya, saida suka daidaita ya juyo ya kalleta yace "Dan ubanki ni kike jira na fara gaishe ki kome? Wai ke me yasa baki da wayo ne?" Saida ta rumgume hannaye ba tare data kalleshi ba tace "Bana da wayon ne, kuma idan kai ka fara gaishe ni miye a ciki indai har kasan darajar mutum." Da k'arfi ya juyo cikin nasara ya finciko wuyanta had'e da hijabinta ya matse sosai yace "Ni kike fad'awa duk abinda ya zo bakinki, sa'anki ne ni? Tambayarki nake?" Yanda ya k'arashe da d'aga murya yasa ta rintse ido tace "Kayi hak'uri to, ina kwana." Turata yayi da k'arfi kanta ya kaiwa kujerar karo, hararanshi tayi shi kuma ya tayar da mota yana baya baya yana fad'in "Shashanci, ita ta raba kanta dani, k'anan nawa ma rabani zatayi dashi, zanyi k'ok'ari na dakatar dashi daga nan, ba zan bari ya ci gaba da faruwa ba, ba zan bari soyayyarshi ta ci gaba da wanzuwa a cikin zuciyata ba, Allah kaine shaida ina ganinshi naji nafi son shi fiye da sauran 'yan uwana, miye laifina a ci? Wane irin virus ne a jikina da har zata nemi nesanta ni dashi? Matsala." Daga Hamna har Amna sun fahimci abinda ke zuciyarshi ne ya fito, Amna kuma dake kallonshi tuni ta ga idonshi sun fara rikid'a alamar kad'an ya rage ya zubo da hawaye, Hamna ma tasan dalilin Ummy kenan tana so ta nesanta shi da d'anshi ne, sai dai kash gashi daga abinda ya fad'a yanzu ta gane soyayyar yaron ta riga data shiga zuciyarshi, haka suka d'auki hanya tana danna wayarta har suka isa. Tare suka shiga wajen Jamila suka dubata, taji dad'in ganinta ita ma dan haka ta saki jiki suka fara hira, ganinsu ne yasa Zeituna da Soueiba suka ce su zauna anan suje gida su dawo, ita Soueiba tana son yin wanka a tsanake saita dawo, Amna ma shiga tayi wajen awo abinka ga masu abun tuni aka gama mata ta dawo, jiransu sukayi dan dama basu zo da niyyar tafiya da wuri ba. *Samun* labarin rashin kunyar da tayi a gidan yasa malam Rabi'u tahowa da ita har gidan, yace dole ta basu hak'uri kuma ba zai ba mijinta hak'uri danya maidata ba, duk da babu yara kuma ita kanta Zeinabu likita take kwana wajen Jamila, amma anyi katarin ta zo saboda zuwan colonel da zai kwana d'aya ya wuce *Mali*, gaban Hajia ya zaunar da ita tace "Dan Allah kuyi hak'uri da rashin kunyar dana muku." Jin wani murmushi da Hajia tayi yasa Maryama d'agowa cikin jin haushi, murmushi ta mata tace "Haba." Cike da iyayi Hajia tace "Ke ni fa abinda kikayi ko a jikina wallahi, kin tona mana asirin da bamu sani bane, dan haka ni banga abun damuwa ba, ban sani ba dai ko ga ita wacce abun ya shafa." Ta fad'a tana kallon Husseina, murmushi Maryama tayi ta kalli Hajia tace "Hajia ke babba ce a gidan nan, babu kyau fariya ga d'an adam bare ke musulma, bai kamata ki dinga tsarkake kanki da ahalinki ba, yaran yanzu ka haifesu ne baka haifi halinsu ba, ko matan baki isa kiyi shaida akansu ba bare mazan, to wai ma akan me kike cika baki? Tare dasu kike fita? Ko kuma kina bibiyar duk abinda sukeyi ne a wajen? ko kuma a cikin gidan kina saka ido akan lamuransu? Ko d'aya fa ba kyayi Hajia, kuma a hakane kike ganin ya zama wajibi akansu su kare kawunansu? To ubangijin daya hallicemu ma ai muna sab'a masa bare kuma ke 'yar adam." Mik'ewa Maryama tayi sai malam Rabi'u cikin barbarci da yace "Mari rashin kunyar ce har a gabana? Lallai kin rik'a." Nuna Hajia tayi tace "Malam ba rashin kunya bane, ita tana ganin kamar iyalinta sunfi k'arfin aikata laifi laifin ma kuma na zina, alhalin bata san tana tare dasu ba kuma suna kewaye da ita." A hankali Hajia ta sauke k'afa d'aya kan d'aya tana kallonta tace "Ban gane ba? Kinsan me kike fad'a kuwa? K'arya kike wallahi." Murmushi tayi tace "Babu maganar k'arya sai gaskiya, ya kamata ki farka daga baccin da kike Hajia ki tabbatar kin gano asalin kowane yaro daya fito daga tsatsonki, dan zai iya yiwuwa akwai yara dayawa wanda aka samu kafin aure kamar irinsu *Junaid*." Zunbur ta mik'e tana kallonta ido a tsaitsaye, da sauri Zeinabu ta dafe bakinta da hannun dama ta daskare a wurin, Husseina Soueiba malam Rabi'u duka sororo sukayi, Junaid kam bai d'auki abin babba ba ganinshi kawai sharri ne, matsowa yayi kusanta yace "Kisan me zaki fad'a Maryama, dan na rabu dake bashi zaisa ki min wannan sharrin ba, ba k'aramin abu bane wannan fa." Tab'e baki tayi tace "Dan ka rabu dani? To autan maza ne kai da zanyi bak'in cikin rabuwa da kai, kaga malam ka tambayi mahaifiyarka ta fad'a maka yanda komai ya faru, karka tsaya kana zare min ido." Malam ta kalla tace "Malam mu tafi, zasuji da matsalarsu." Tashi yayi yana waiwayen Husseina da shi dai yake son neman yafiyarta, suna fita colonel da lieutenant suka shigo tare da Alhaji cikin farin ciki, suna ganin yanayin mutanen wurin kowa yayi sororo ga Junaid yasa Zeinabu gaba yana magana k'asa k'asa yasa lieutenant k'arasawa da sauri wurin Hajia yace "Hajia lafiya? Meya faru duk na ganku haka?" Colonel ma matsawa yayi kusanta yana karantar tsantsan tashin hankali daka fuskarta yace "Hajia lafiya?" Dab'as ta zauna kan kujerar da kullum take jin dad'in zama kanta cikin isa da izza, duk yanda numfashinta ya fara barin gangar jikinta saida tayi k'arfin halin kallonshi cikin fitar da numfashi sama sama tace "Husseini..da gaske...ne.Ju...Junaid baaaa..." Kasa k'arasawa tayi wanda hakan yasa colonel sunkuyar da kai, *wal'iyazu billah* shine abinda ya fad'a à ransa, kamar an jonata da kuran sai kawai ta tashi tsaye da k'arfinta, hannu ta d'aga sama da niyyar palla masa mari, sai kawai jikinta ya d'auki b'ari hannunta ya fara rawa da k'arfi kamar ta kama wayar lantarki, lieutenant da colonel d'in ne sukayi azamar rumgumata a jikinsu cikin tashin hankali lieutenant "Mu kaita mota." Da gudu Zeituna ta k'araso tana k'ok'arin rik'eta tace "Ku saketa zamu kamata." Soueiba ce ta taso da sauri suka kamata su kuma suka nufi mota, ana fita da ita sai asibiti wajen su Ammar, ganinsu ya d'aga musu hankali suma ba kad'an ba, Ammar da Ummy da kuma wata malamar asibiti ne suka rufa kan Hajia aka fara k'ok'arin ceto ranta. *Awa biyu* suka d'auka kafin su fito fad'a musu halin da take ciki, Hajia kam dai... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _49_ Ammar ne yace "Cikin sarautar Allah komai ya daidaita, jininta ne ya hau sosai, amma yanzu mun samu mun shawo kan lamarin, ba wata bazarana a yanzu zaku iya komawa da ita gida, akwai magunan da za'a bata ta samu bacci." Alhaji ne yace "Ammar kana ganin zamu iya tafiya da ita gida tun yanzu? Me zai hana ba zaku barta nan ba ta samu ta huta." Dafa shi yayi yace "Ba komai Alhaji zaku iya tafiya da ita, kuma ko da wani abu ya faru ma ba gani ba duk da bama fatan haka." Sallamarta sukayi tare da Jamila ita ma amma sun rigasu tafiya, ko da aka je gida d'akinta suka kaita aka bata magani tasha, ba jimawa bacci ya d'auketa idonta na kan colonel da take matuk'ar son marin fuskarshi, suna ganin bacci ya d'auketa kowa ya sauke ajiyar zuciya, a tsanake Alhaji ya kalleshi yace "Husseini shin gaskiya ne abinda aka fad'a d'in?" A hankali ya sulale ya durk'usa gabanshi duk da babu hawaye a idonshi amma muryarshi na rawa yace "Alhaji kuyi hak'uri ku gafarceni, kuskure na wallahi, hakan ya faru tun kafin a d'aura aurenmu, ta so na fad'a asan halin da ake ciki amma, Alhaji ina jin tsoron Hajia sosai, tsoron abinda zatayi yasa muke b'oye wannan sirrin har wannan lokacin, amma wallahi kullum da fargaban hakan muke kwana kuma muke tashi." Ajiyar zuciya Alhaji ya sauke ya kamo shi ya tashi, kallon idonshi yayi yace "Husseini, ba'a gyara kuskure da kuskure, shiru ba shine mafita ba illa ma ya k'ara haifar da wata matsala, na so ace a lokacin ko ni ka tuntub'a da lamarin dan asan abunyi, abinda kukayi kuskure ne, kuskurenku ma akan kuskure kukayi shi, yanzu kaga me hakan ya haifar? Shi yaron da wane ido zai kalleku?" A hankali ya d'aga kai ya kalli Junaid dake gefenshi, Zeinabu dama bata tafi asibiti ba saboda tafi Hajia ma shiga tashin hankali, kawai ita nata ya fito fili ne aka gani, k'yar kam idonshi cikin na shi, kallon babu wanda yasan na miye ma kawai suna kallon juna ne, cike da dattako Alhaji ya kallesu dukansu yace "Yanzu dai tunda haka ta faru kawai komai ya wuce, Junaid hak'uri zakayi wannan ita ce jarabawarka, kai kuma kai da ita sai kuyita istigfari wajen ubangiji, abun kuma a bud'e yake cewa yanzu shi ma magajinka bane." Saida ya sunkuyar da kai yace "Allah ya kyauta ya kuma kiyaye gaba." Saida ya goya hannayenshi baya ya fara tafiya ya fita daga d'akin, da sauri Junaid ya bi bayanshi da alama kuka ya fashe dashi, ajiyar zuciya lieutenant ya sake saukewa mai k'arfi, shima fita yayi tare da Ummy data baro asibitin suka taho tare. Ko da aka dawo Jamila tace a mata shinfid'a a d'akinsu na yan mata, a lokacin babu wanda ya kula saboda duk jikin kowa yayi sanyi *gwamnatin* gidan babu lafiya, ga kuma zulumin abinda ya faru da mamakin al'amarin, can aka gyara mata ta zauna ita da jinjirinta, basu kula ba saida Jibril ya zo yana tambayar inda take kad'ai aka gano, Soueiba da Husseina ne sukayi ta bata baki amma ta rufe ido ta botsare tace ita fa ta gama zaman gidan shi, k'yaleta sukayi da tunanin idan ta huce sai a mata magana ta koma. Tunda Zeinabu ta shiga d'aki ta kasa fitowa sai dai colonel ya shiga kawai ya fito, sai kuma Zeituna dake kai mata abinci ta aje ta fito. Haka kuma ita ke kula da Hajia tunda ta farka da la'asar, da taimakonta tayi alwala tayi sallah, da hannunta ta bata abinci tasha magani. Bayan sallah magriba lieutenant ya shirya cikin kakin shi ya fita, oda ya bayar tare da rahoto akan motar cewa a dakatar da ita, kafin a sanar dashi ganin motar wasu abubuwan ya shiga yi, sai misalin *11:40* aka kirashi aka fad'a mishi ga motara hannu d'auke da kaya, nan yayi umarni aka taho da ita har ofishinsu inda ya fito da kanshi bayan anshiga da ita ciki, saida ya gama kallonta ya ga sak kwatancen da Ammar ne ya masa, nan yasa yaransa suka bud'e motar aka fara fito da kayan ciki, dreban na gani ya fara fad'in "Ba fa komai bane yallab'ai, indomie indomie ce sai madara." Wani kallo lieutenant ya masa yace "Ka bari to mu gani da kanmu." Pilla pilla lieutenant yasa aka ma kayan nan, sai gashi karton d'in da ake tunanin indomie ce ciki da kwalayan madara an samu tramol a ciki, haba ai sai hankalin dreba ya tashi dan baisan abinda ya d'auko ba, mai kayan aka sa shi ya kira sai ga Jano ya zo ya d'auka kamar yanda aka saba ne, idan aka rik'e kayan ko kuma aka musu awo a caji kud'i masu yawa, sam basu sarara masa ba hannun jami'an tsaro suka mik'ashi tare da dreban, sai dai shi daya rantse baisan menene ba kuma ya fad'i yanda akayi ma har ya d'auko kayan sai suka gamsu, musamman da shi kanshi Jano d'in ya tabbatar musu da babu ruwan dreban, shi ma kuma cewa yayi ba kayan sa bane, abu dai yaja daga an sake dreba Jano kuma yau gashi da kwanan magark'ama. Da dare tana zaune ita kad'ai a d'akin ta had'e fuska, tunani take irin matakin ma da zata d'auka na wannan cin zarafi da Husseini ya mata, ita zai kunyarta ya wulak'anta a idon duniya, tana kalkad'a k'afa alamar masifa Zeituna ta bud'a k'ofar ta shigo da sallama, saida ta zo har ta aje kwanukan abincin zata fara zuba mata tace "Dakata malama bana so, fice min a d'aki." Da ladabi ta kalleta tace "Hajia lokacin shan maganinki yayi fa." "Nace bana so ki fitar min a d'aki." Sake k'asa tayi da muryarta tace "Dan Allah Hajia ki daure..." Tsaye ta mik'e ta nuna mata k'ofa tana fad'in "Nace ki fita ko, ko saina sa an fitar min dake ne?" Juyawa tayi cikin sauri sauri ta fita, da harara ta bita duk sai take jin haushin matan ma, kawai ita bata yarda dasu ba, dan haka sai kowace ta fito mata da d'an da ba jininta ba, inba haka ba duk saita kaisu asibiti an gwada uban kowa dan tasan yaran da suka ciyar a banza. Tana cikin safa da marwa Ammar ya shigo da siririyar sallama, tana juyowa ta ganshi ranta ya sake b'acewa tace "Fitar min a d'aki kaji, bana son kowa ya sake shigo min d'aki ina buk'atar zama ni kad'ai." Rufe k'ofar yayi ya tako da sauri yana fad'in "Hajia ta nayi kewarki fa." Cakumota yayi ya rumgume da k'arfi yace "Kin tsoratani fa sosai, ban tab'a yarda cewa ana jin k'amshin lahira ba sai yau dana kusa rasaki." Tureshi tayi daga jikinta cikin tsawa tace "Kana hauka ne? Ammar fice min a d'aki kafin ranka ya b'ace." Hannunta ya kamo ya zaunar da ita bakin gadon ya fara zuba abincin yana fad'in "Ba zan yarda ki sake min wasa da lafiyarki ba, Hajia dole sai kinci abinci kafin kisha magani, inba haka ba zansa Alhaji ya rik'e min ke mu miki d'ure." Zaune yayi bayan ya gama zubawa ya d'ebo a cokali ya kai bakinta, k'ank'ance idonta tayi tace "Baka da hankali ne Ammar?" Kai ya d'aga mata yace "Eh Hajia ta, akan ki mahaukaci ne ni." "Shin baka fahimtar abinda nake fad'a maka ne?" Saida ya turo baki yace "Ai ba zan fahimta ba har abada." Cike da k'aguwa tace "Akan me to zaka nuna ka damu dani bayan nasan ba so na kake ba kamar yanda bana sonka?" Murmushi ya mata yace "Saboda bana so na rasaki." Kallon idonshi tayi tace "K'arya kake Ammar, nasan zaka fi kowa murna idan na mutu." "A'a Hajia, zanfi kowa bak'in ciki." Ya fad'a shima yana kallon k'wayar idonta, cikin taushin murya tace "Me yasa?" Ba tare daya d'auke idonshi ba yace "Saboda zanyi kewar masifarki, zanfi kowa damuwa na rasa babbar mai yi min fad'a da zagina da kuma yanke hukunci akaina ba tare da shakku ko shawartata ba." Me Hajia zatayi ba dariya ba, ita kanta ji tayi ta taho mata, bata san me yaron nan yake ji dashi ba da har yake iya tunkararta ya fad'a mata abinda ke ranshi ba tare da shakku ba, ita yake kallon idonta yake fad'a mata wai zaiyi kewar *masifarta*, ba tare data tsagaita da dariyar ba tace "Ammar kai mahaukaci ne." Yana kallonta yace "Na sani Hajia, haka kuke fad'a kullum." Lomar ya mik'o mata sai kawai ta harareshi tace "Ban ci nace ko." Langab'e kai yayi yace "Hajia jan ajin ya isa haka mana." Wata dariyar ta sakeyi ta kamo hannunshi ta zura lomar bakinta, kallon bakinta yake yanda take tauna abincin yasa yake hango k'uruciyarta, abun mamaki shine karb'an abincin da Hajia ta dinga yi daga hannun Ammar kai kace dama can haka suke, shi kanshi sai yake jin abun na daban bai saba ba, duk da bata ci sosai ba haka ya aje ya bata magani tasha, tana sauke kofin daga bakinta ta kalleshi, haka kawai taji kamar kunyarshi na son lullub'eta ba gaira a dalili, aje kofin tayi a hankali ta d'ora goshinta kan gwiwarshi ta sauke ajiyar zuciya tace "Ammar kaga abinda kawunka ya min ko? Kaga irin k'ask'ancin daya ja min? Kana ganin irin tozarci da zubar da mutumcin daya min? Wane irin mataki ne zai d'auka akan shi? Akan me zasuyi min haka saboda kawai ina son kare iyalina." Cikin murmushi ya k'ara jawo kanta saman cinyarshi yana wasa da yatsun hannunta yace "Hajia na fahimci duk k'ok'arinki na son karemu ne daga aikata abinda bai dace ba, amma kuma tsananin da kikayi ne yasa iyalinki ke matuk'ar tsoronki, Hajia idan kana son yaro ya saba da kai ya dinga jin maganarka ba tsanani ke sa haka ba, jawo shi a jiki da wasa da shi da kuma durmiya cikin al'amuranshi, shi ke sa ba mace ba har namiji ya saki jiki da kai yana fad'a maka sirrinsa, Hajia ni baki gani ba har yanzu bana iya wani sirri da mahaifiyata ba, Abba ma yanzu ne kad'ai na fara fad'a masa damuwata, ke ma hakane Hajia ya faru da ke, da ace tun farko kinsa iyayenmu a jikinki kin nuna musu so da k'auna wallahi da sanda abin nan ya faru kawu zai sanar dake ko da yasan ranki zai b'ace, kiyi hak'uri Hajia idan abinda na fad'a ya b'ata miki rai." D'agowa tayi ta kalleshi ido cikin ido tace "Ammar me kake nufi? Wace irin soyayya ce zai nuna musu da ban nuna musu ita ba?" Murmushi yayi yace "Hajia kina son 'ya'yanki sosai mana, saboda kin haifesu haihuwa kuma ba wasa bace, matsalar d'aya ita ce ba kya nuna musu soyayyar a zahiri." Wani dogon tsaki taja ta gyara zamanta tace "Ban gane me kake nufi ba, kawai ka fitar min a d'aki." Murmushin gefen labb'a ya mata ya mik'e tsaye yana kallonta yace "Zan fita Hajia, amma kiyi tunani akan abinda na fad'a miki, domin kuwa na fi kowa son ganin kan gidan nan ya had'u." Har ya juya sai kuma ya tsaya ya juyo yace "Ban san ko zaki iya tuna ranar k'arshe da kika tab'a bin iyayenmu da addu'a ba ta alkairi, misali idan sun miki alkairi ko zasu fita aikinsu ko kuma zasuyi balaguro, Hajia ke a ganinki duk abinda suka miki abune dama da yake wajibi akansu dan haka babu buk'atar kiyi musu godiya ko addu'a, Hajia kina ganin kin haifesu kin gama musu komai a rayuwa, dan haka ya zama dole akansu suyi duk abinda kike so, amma kina mantawa da ubangijin daya hallicesu kuma ya halliceki, to Hajia ko ubangiji yana bawa bayinsa wata dama, wannan damar kuwa ita ce talala da yake mana dan mu tuba ga laifikanmu, amma ke..." Girgiza kai kawai yayi ya fita daga d'akin, da kallo ta bishi da mamaki, to wai akan me yake magana? Soyayya? Addu'a? Jansu a jiki? Tsanani? Tab'e baki kawai tayi ta jinjina kai tace "Dan na saki jiki da kai shine har zaka fad'a min magana." Zaune suke a falon sama suna hirar da babu nishad'i a ciki sakamakon abinda ya faru, Zeinabu ma ko fitowa ba tayi ba bare ta gansu taji kunya, Hamna na gefe d'aya k'asan carpet ta mik'e k'afafu, Shureim ma na nesa dasu saboda k'arfin pankar da suka kunna saboda guje mishi kamuwa da mura, motsawa yayi tare da fashewa da kukan daya shiga duka kunnuwan iyayen nashi biyu, autar Soueiba *Basira* ce tayi karanbanin rugansu d'aukoshi, yanda ta d'auko shi ba daidai ba yasa Hamna zabura daga zaman da take da gudu har tana take rigarta ta nufeta, tana zuwa ta rumgoshi jikinta ta karb'eshi tana kallon Basira tace "Uban wa yace ki d'aukeshi, sai kin ji masa ciwo hankalinki zai kwanta, baki ga jikinsa baiyi k'wari bane da zai juri wannan wahalar." Tsaki tayi cike da jin haushi har zuciyarta ta juyo da niyyar zaunawa, saida ta zabura ganin Ummy ita ma ta taso a bayanta tsaye tana kallonta, wani kallo ta mata mai cike da gargad'i sannan ta karb'eshi ta koma ta zauna, gabanta fad'uwa kawai yake tana satar kallon su Soueiba da Zeituna, su dai abun ya basu mamaki na saurin zaburar da tayi kamar daga cikinta d'an ya fito, amma bayan haka basuyi tunanin komai ba, Hamna na zaunawa wayarta tayi k'ara, dubawa tayi taga Amna ce, d'auka tayi sai kawai tace "Dan Allah yer uwa ki zo." Wani iska ta furzar dan ita fa bata so tana kusantar da kanta gare shi, bata so tana ganinshi akai akai wani abu take ji, tabbas kuma ba tsana bace sai dai tana jin haushinshi, kashe wayar kawai tayi ta gyara zaman kallabin doguwar rigarta ta fita. Tana saukowa ta zo tsakiyar falon shima ya fito daga d'akin Hajia, a tare suka kalli juna da sauri ta d'auke na ta idon ta k'ara sauri dan ta fita, shima kuma cikin takon sauri yake dama shiyasa suna ka kai daf da k'ofar a tare, zata fita ba tare data bari ya wuce ba shine abinda ya bashi haushi, tsayawa yayi ya mata wani irin kallo yace "Wuce uwata." Wani kallon sama da k'asa ta masa ta fice kam abinta, a baya ya binta yana kallo kuma ita ma can ta nufa, kawai baya jin masifa ne amma da saiya gabza mata mari ko ta koyi girmama shi, tana shiga ta sameta zaune k'asa kamar kullum, jin takonshi a bayanta yasa ta d'aure fuska tace "Me zan miki da kika kirani?" Turo baki Amna tayi tace "Shikenan fa tunda muka dawo daga asibiti baki zo kika dubani ko ina lafiya ba." "Akan haka kika kirani?" Gira ta d'aga mata kawai, juyawa tayi tace "Saida safe." Da kallo kawai ta bita haka shima, zaune yayi kusan Amna yace "Yarinyar can k'uruciya na damunta." Kallonshi tayi tace "Tana damunta ko tana damun mu?" Saida ya rumgumota jikinshi yace "Ai ke kin kusa girma da zaran kin fara aje min yara." *Da safe* Alhaji na zaune ya zo dubata colonel ma ya shigo dan yana son yin sammakon komawa, sallama yayi Alhaji ya amsa, saida ya kai har k'asa cikin tsananin ladabi ya gaishesu, Alhaji dai ne ya amsa banda Hajia dake kallonshi, yana d'agowa suka had'a ido yayi saurin sauke kanshi k'asa, shiru ne ya d'an ratsa d'akin kamar anyi sabuwar mutuwa, ganin dai ba zatayi magana ba yasa ya kalli Alhaji yace "Alhaji zan koma ne dama." Cikin dattako yace "To Husseini, Allah ya tsare ya kiyaye." "Ameen nagode." Ya fad'a yana kallon Hajia yace "Hajia zan..." Saida ta d'ago daga jinhinar da tayi cikin katse hanzari tace "Wallahi ranka zai mugun b'aci idan ka ambaci suna na." Marairaicewa yayi kamar yaro yace "Hajia dan Allah kiyi hak'uri ki yafe mana." Saukowa tayi daga gadon tace "Akan me zan yafe maka? Husseini kasan me ka aikata kuwa? Ni zaka wulak'anta." Alhaji ne ya mik'e tsaye ya kalleshi yace "Kaga tashi, tashi ka tafi inda zaka Allah ya kiyaye hanya." D'aga kai yayi ya kallesu duka saiya kasa tashi, cikin d'aga murya Alhaji ya sake cewa "Ka tashi ka tafi nace." Mik'ewa yayi yace "Na tafi." Yana fita Hajia ta kalleshi cike da jin haushi tace "Wai me yasa kake min hakane? Ya zanyi magana dashi kawai ka wani ce ya tafi? Ina ruwanka to da abinda zamu tattauna? Meya hana kai ka fita idan ba zaka sauraremu ba." "Dakata Zeeya'atu." Ya fad'a yana d'aga mata hannu, d'orawa yayi da "Da alama har yanzu baki san annabi ya faku ba, to ki bud'a kunnenki da kyau ki saurareni, babu wani hukunci ko matakin da zaki d'auka kan lamarin nan, dukanmu zamu duk'ufa ne mu nemi gafarar ubangiji kan zunubanmu, dan idan da wanda yayi sanadiyar faruwan hakan to ke ce." Nuna kanta tayi tace "Ni? Ni fa kace! To me nayi ni d'in? Ce musu nayi su aikata? Ko kuma ina wurin sanda suka aikata bare ya zama laifina ne dana barsu suka aikata." Saida ya tsaya daf da ita yace "Ke kin manta abinda ake fad'a ne cewa duk abinda kayi shi za ayi maka?Ai indai zakayi d'in to fa ka kwana da shirin sai an maka." Rarraba ido ta fara yi alamar rashin gaskiya, sai kuma ta nad'e tabarmar kunyarta da hauka tace "Ban gane ba? Kana nufin nima nayi ne ko?" Dariyar kin raina min hankali ma ya mata yace "Ni bance ba, amma dai ki sake kula ki kuma nemi yafiyar ubangijinki, idan ba haka ba wallahi yanzu irin abunuwan nan suka fara faruwa, kuma ki sani su ne zasuyi ajalinki, dan haka zaifi kyau ki koma ga Allah ta yanda in mutuwar ma ta zo ki cika da imani cikin kyakyawan yanayi." K'wank'wasa k'ofar suka ji anyi wanda yasa su kallon k'ofar, Alhaji ne yace "Shigo." Ammar ne tare da Amar da Amna da kuma Jibril, da sallama suka shigo dukansu, gaishesu sukayi sosai kafin su kalli Hajia su ce "Ya jiki?" Saida ta wani d'aure fuska tace "Da sauk'i." Ammar ne yace "Hajia kin karya kuwa?" Girgiza kai tayi alamar a'a, juyawa yayi yana fad'in "Ya kamata ki daina jinkirin nan fa." Amna ce tayi saurin cewa "Yah Ammar bari na karb'o." Tsayawa yayi ita kuma ta fita, Alhaji ne yace "Ina Junaid yake?" Amar ne yace "Anya Junaid ya kwana gidan nan kuwa? Dan ni dai jiya sai dare sosai na shigo amma banga motar shi ba, yanzu ma kuma babu motarshi a wajen ajiyewa." Kai Alhaji ya girgiza, Amar ne ya fara mik'ewa yace "Zan wuce ni lokaci na tafiya, Hajia Allah k'ara sauk'i." Saida ya mik'e tace "Shalele ka zauna tare dani mana, kai kad'ai nake son gani a kusa dani, wasu banda b'ata min rai babu abinda suke yi." Ta k'arashe maganar tana kallon Alhaji da kuma Ammar, murmushi dukansu sukayi sai Amar da yace "Kiyi hak'uri Hajia, wallahi akwai aiki sosai a ofishi, amma na miki alk'awarin zan dawo da wuri sai na zo mu zauna." Murmushi ta masa tace "To karka manta fa, saika dawo." Ficewa yayi Amna kuma ta shigo, Jibril ma tashi yayi ya fita haka ma Alhaji, yau ma kamar jiya da kanshi ya zuba abincin ya zauna kusa da ita ya fara d'ebowa a cokalin ya nufi bakinta, kawar da kai tayi tace "Bani zan ci da kai na." Girgiza kai yayi yace "Idan da kanki ne ba zaki ci dayawa." Sake tura mata cokalin yayi ta bud'a baki ta karb'a, yana cikin bata Ummy da lieutenant suka shigo tare, su ma gaishe ta sukayi da tambayar jikinta ta amsa ba yabo ba fallasa, kallonta Ammar yayi ya d'an sunkuya yace "Baki tambaye su Shureim ba." Kallonshi tayi amma yanda yake kallonta yasa taji ta kasa masa gardama, kallon lieutenant yayi dake rik'e dashi kamar zata bud'a baki sai kuma ta ga ai ba girmanta bane sai kawai ta sake kawar da kanta, Ummy da lieutenant mamaki suke sosai har da Amna ganin wai Hajia ce ke karb'an abinci daga hannunshi, da wannan mamakin Ummy tace "Hajia Allah k'ara sauk'i, zan tafi gurin aiki amma ba zan jima ba saboda na dawo kusa dake." Ko kallonta ba tayi ba harta fita, lieutenant ma sallama ya mata suka fita, Amna ce ta kalleshi tace "Yah Ammar zan duba Hamna na dawo." Kai ya jinjina mata ta fita, saida ya gama bata ya bata maganin tasha ya mayar da komai ya aje sannan ya kalleta, cikin dakakkiyar murya yace "Hajia gaskiya Alhaji ya fad'a miki, akwai buk'atar mu tuba ga Allah." Ya fad'i hakane saboda sanda ya riga kowa isowa bakin k'ofa yaji kalamanshi na k'arshe cewa *"Dan haka zaifi kyau ki koma ga Allah ta yanda in mutuwar ma ta zo ki cika da imani cikin kyakyawan k'arshe."* Ido ta zaro tana kallonshi, duk tsoro ya bayyana tare da ita tace "Me? Ammar lab'e kake mana dama?" Murmushi ya mata yana girgiza kai yace "Banda wannan lokacin Hajia, watak'ila Allah yasa na jini saboda akwai abinda zan iya yi akai." "Me kaji d'in?" Ta fad'a idonta a waje, saida ya had'e dariyarshi ya kalli idonta sosai yace *"K'uruciyarki, rayuwarki ta baya Hajia, wacce babbu wanda yasan da ita sai Alhaji sai kuma ni da naji yana fad'a a cikin addu'o'inshi."* Cikin rawar hannu ta d'oki hannunta na dama ta rufe baki da taji numfashinta na neman gagararta, a hankali a hankali ta fara lumshe idonta da taji kanta na juyawa tare da sara mata, mik'ewa yayi ya kwantar da ita kan matashi, yatsu biyu yasa ya dafa kanta inda yaga tana dafewa da hannu, bud'a jakarshi yayi ya fara dube dube, da k'arfi ya d'aga daga sunkuyawar da yayi yace "Shiit." Da gudun bala'i ya juya ya fita, kamar wanda kura ta biyo haka yake gudu har wanda suka ganshi suka tsaya kallonshi, b'angarensu na samartaka ya shiga cikin sauri yake bud'a kowane d'aki ya shiga, d'akin magungunanshi ya shiga cikin sauri sosai ya d'auko kwalin wata allura da abin k'arin numfashi (oxygène) haka ya rumgumoshi a jikinshi ya sake fitowa da gudu. Yana shigowa ya sameta yanda ya barta sai jan numfashi take, cikin gaggawa ya samu wuri ya aje bunburutun oxygène d'in ya jona ya saka mata, wasu allurai ya had'a yasa a ciki take wani iska ya dinga taimakawa Hajia wajen numfashi inda daga k'asa kuma wasu ruwa ke ta tafasa, k'ura mata ido yayi yana kallo sannu sannu numfashinta ya fara saisaituwa, ajiyar zuciya ya sauke tare da jawo kujerar gaban madubinta ya zauna yana kallonta, Zeituna ce ta shigo da sallama ya amsa, kallonta yayi yace "Uwa antashi lafiya?" Tana kallon Hajia tace "Antashi lafiya? Ya kuma naga an sa ma Hajia wannan?" Kallonta yayi shima sai kawai ya bushe da dariya yace "Kin ganta nan fa sai alamun margaya take nunawa." Duk da tana lumshe ido bacci na son d'aukarta saida ta kalleshi, hannun dake kusa dashi ta d'aga mishi tana son kama nashi hannun, da sauri ya had'a hannunshi da na ta, da alama magana take so tayi sai kuma ta fara lumshe ido, a haka kuma bacci ya d'auke ta ya saki sannunta, haka kawai yaji ba zai iya yin nisa da ita ba a halin da take ciki, dan haka ya kira asibiti ya fad'a musu yana da wani marar lafiyar da yake dubawa, duk wanda zai gani yau a basu rendez vous da yamma. Sosai Labaran ya mishi fad'a da nuna baiji dad'in abinda ya faru ba, Soueiba dai abinda ta fad'a mishi shine, tunda hakan ya faru da farko dai ayi hak'uri tunda ba jiya ko yau bane haka ta faru ba, sannan su rik'e yarinyar su kula da ita tunda dai dama duk yan uwa ne, a banza ma zasu iya rik'eta bare kuma jikanyarsu ce, na biyu kuma Jamila dake ikrarin ya rabu da ita suyi k'ok'ari su ga auren bai mutu saboda wannan matsalar, da haka ta kwantar masa da hankali suka fuskanci gaba. Bai fita ko ina ba sai wayarsa da yake dannawa yana gudanar da harkokin daga nan zaune, agogon hannunshi ya kalla sannan ya kalli Hajia, tabbatarwa da yayi daga yanzu zuwa kowane lokaci zata farka yasa shi fita daga d'akin ya fito, a falo ya gansu zaune suna ta hira abinsu cikin raha, fuska a had'e ya kalleta yace "Ke had'a ma Hajia abinda zata ci, amma kada kisa arôme (d'and'ano) tare da abinsha naturel." Kamar bata ji ba dan haka ya sake kallonta yace "Dake nake fa." Saida ta harari gefenta ta mik'e tana fad'in "Sai kace banda suna wani wai ke, menene ma'anar ke?" Kallonta yayi ya cije leb'en k'asa, zai matso kusanta ta rufa da sauri ta shige madafar, dariya Amna tayi ta girgiza kai tace "Naga ranar da zaku girma." Kallonta yayi yace "Amna nine ban girma ba? Ni kike had'awa da waccen yarinyar? Ni Amna?" Kanta yayi kamar zai mazgeta hakan yasa ta rufe fuska da hannaye cikin muryar kuka tace "Kayi hak'uri to ba kai ba, ni ita nake nufi." Dariya yayi ya sunkuya ya sumbaceta ya juya ya koma d'akin Hajia, minti arba'in ta d'auka kafin ta shigo d'akin da sallama, d'agowa yayi yana kallonta har ta shigo ta aje farantin hannunta, juyawa tayi zata fita yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _50_ "Uban waye zai zuba miki?" Juyowa tayi ta murgud'a baki tace "Kai musaki ne?" Tattare rigarta tayi ta tafi a guje, takon da baifi uku ba ya rik'o wuyan rigarta da k'arfi yayi baya da ita, k'ara tayi wacce tasa Hajia k'arasa bud'e idonta ta kallesu, hannu ya d'aga da niyyar kasheta da mari, amma me sai yaji ba zai iya tab'a lafiyar jikinta har haka ba, tsaki ya ma kansa kafin yasa k'arfinsa ya damk'i gashinta yana fad'in "Sa'anki ne ni?" K'ara tayi tare da rintse ido tana k'ok'arin cire hannunshi a kanta, hannu ya d'aga kamar zai mareta, da sauri ta rik'e k'afarshi cikin kuka tace "Yi hak'uri to zanyi, zan zuba, zan zuba wallahi, dan Allah yi hak'uri." Da k'arfi yace "Tashi to." Tashi tayi ta dawo inda ta aje kwanukan ta fara zubawa, saida ta gama ta mik'a mishi tace "Gashi." D'aga idonshi yayi ya mata wani kallo yace "Aje a kaina." Saida ta turo mishi baki kafin ta aje gefen gadon, juyawa tayi saida ta bud'a k'ofar tayi shirin rufeta sannan ta zuro kai tace "Allah ya saka min cutar daka min." Tana fad'a ta ari na kare, cikin nutsuwa ya bita da kallon rashin fahimta, cutar daya mata? Wace cutar kenan? Abinda ya faru baya ko kuma yanzu? Tab'e baki yayi ya mik'e ya kama Hajia ta tashi, saukowa tayi daga kan gadon yana rik'e da hannayenta, ta mik'e tsaye Zeituna ta shigo da sallama, da sauri ta k'araso tana kwance goyon Fatima ta aje kan gadon tace "Yah Ammar bari na kaita." Sakinta yayi suka shiga ban d'aki shi kuma ya d'auki Fatima yana mata wasa, baki kawai ta wanko ta fitota koma ta zauna, ita ta zuba abinci ya bata da kanta ta ci tasha lemu, maganin ya bata ta bata sannan yace ta d'an zauna, amsar Fatima tayi suka fita dan aikin gabanta, kallonta yayi shima yace "Hajia nima zan tafi asibiti yanzu, dan Allah kada kiyi wasa da magunan nan." Ya fad'a yana nuna mata su, juyawa yayi zai fita tace "Ammar zo." Juyowa yayi ya tsaya ta nuna masa kusa da uta tace "Zauna mana." Zaunawa yayi yana kallonta, saida ta sunkuyar da kanta tace "Ammar tun yaushe kasan da haka kuma baka fad'a ba kowa ya ji?" Da mamaki ya kalleta yace "Subhanallah! Hajia na fad'a? Na fad'a ma wa to?" Kallonshi tayi tace "A gani na k'iyayya na nuna maka, shiyasa nake tunanin ko zaka iya fad'a dan ka kunyata ni." B'ata fuska yayi yace "Haba Hajia, ke fa kakata ce wacce ta haifi abun tutiyata, taya zan miki haka? Hajia duk abinda kike min gaskiya ne ina jin zafi a zuciyata, amma kuma bana rik'e ki ta yanda har zanyi tunanin d'aukar fansa a kanki ko kunyata ki, Hajia duk da kina fad'a min gaba da gaba cewa baki sona ni ban tab'a yarda ba, abu d'aya da nayi imani dashi shine babu wanda zai k'i nasa sai dai ya k'i wani halinsa." Jinjina kai tayi alamar gamsuwa kafin tace "Tun yaushe kasan da maganar nan Ammar kuma kayi shiru?" Murmushi yayi yace "A k'alla wata goma yanzu, wani dare ne naji yana fad'a tsakaninshi da mahalincinsa, dare ne da ni kaina ya shiga cikin tarihin rayuwata, domin abinda ya faru a daren bayan naji abinda ya fad'a ne ya tabbatar min da lallai duk abinda magabatanmu suka aikata yana iya dawowa kanmu, sannan na tabbatar da abinda ya fad'a miki yanzu cewa dole sai kin tuba Hajia, inba haka ba akwai wasu abubuwan da zaki k'ara ji nan gaba wanda a gaskiya zasu iya k'arasaki ga kushewarki." Abun mamaki da al'ajabi, abunda ko a mafarki baiyi tsammani ba shine ya faru, Hajia Zeeya'atu, Hajia dai sarauniyar izza ji da kai tak'ama da alfahari, ita ce wai ke kuka da idonta tana rik'e hannunshi tana fad'in "Ammar ka fad'a min dan Allah me yake faruwa a cikin iyalina? Ammar na fara jin tsoro, sai nake ganin kamar shashashar uwa ce ni." Da sauri yace "A'a Hajia, ke uwa ce tsayayya kan iyalinta, Hajia akwai wuya samun uwa kamarki, ba kowace uwa bace ke tsayawa har kan tarbiyar jikokinta ma bayan ta tarbiyaccin 'ya'yanta, kawai dai yar matsala ce aka samu daga wani wurin." Ba tare data saki hannunshi ba tace "Ka fad'a min Ammar idan kasan wani abu dake faruwa, dan Allah ka fad'a min kaji." Girgiza kai yayi yace "Hajia bana so hankalinki ya sake tashi, k'azantar da baki ganta ba kuma baki jita ba tsabtace a gareki." Cikin kuka mai matuk'ar nuna nadama tace "A'a Ammar ka fad'a min zan d'auka, zunubi na ne bai kamata ya shafeku ba, nayi alk'awarin tuba ga Allah abisa cin amanar mahaifina da nayi da kuma zina, zan rok'i Allah ya yafe min zubar da cikin dana tab'a yi, dan Allah ka fad'a min Ammar ko zan samu na nemi iyalina gafara." Da k'yar ya iya b'oye tashin hankalinshi da tsoron al'amarinta, shi bai ma san ta zubar da ciki ba sai yanzu, lallai abun azimun ne, shirun da yayi yana kallonta yasa ta kalleshi tace "Ammar yanzu ne na fahimta banda masoyi a duniyar nan sama da kakanka, ashe duk yasan da abun nan kuma bai tab'a nuna min ko ya fad'a min ba, duk irin rashin mutumci da wulak'anci dana masa..." Kuka ne ya k'wace mata ta sunkuyar da kai tana kuka, saida ta nutsu ta d'ago tace "Da wane ido ne zan dinga kallonshi yanzu, Ammar babu irin k'ask'ancin da ban mishi ba a rayuwa, a rayuwar aurenmu nasan akwai lokacin da yayi farin ciki, amma bak'in cikin da yayi ya ninka farin cikin sau ninkin ba-ninkin, duk da yasan lagona yasan makullin ruguza duk wani gidan rashin mutumcina amma bai bud'e ba, Allah sarki bawan Allah, wannan dalilin ne yasa nake k'ara son shi kullum, *hak'uri*, yana da matuk'ar hak'uri." Murmushi yayi yace "Hakane Hajia, amma ki gode Allah da yasan kika fahimci haka tun dukanku kuna raye, kinga kenan akwai damar neman yafiya da gyara kuren gaba." Kallonshi tayi tace "Hakane Ammar zanyi, amma dan Allah ka fad'a min idan kasan akwai wani abu daya kamata na sanshi?" Shafa gemunshi yayi yana nazari, sake matsowa yayi kusanta ya rik'o hannunta yana kallon idonta cikin bin kowace kalma daki-daki yace "Hajia, bansan komai a game da kowa ba sai wanda ke fitowa yanzu, kaina kawai na sani." Bakinshi ta k'urawa ido tana kallo kamar mai son fahimtar yarenshi tace "Ka aikata wani abu ne kai ma daya kamata na sani?" A hankali ya jinjina mata kai alamar eh ba tare daya rusuna idonshi daga kan fuskarta ba, cikin zak'uwa tace "Meye? Me ka aikata Ammar? Kenan pentina ya shafeka?" Kai ya fara jinjina mata tare da cewa "Eh, Hajia nawa yafi na kowa muni, kowa abun bai faru dashi da wani na shi ba, amma ni da yer uwata haka ya faru, wacce muka tashi tare uwa d'aya ta rainemu, da ita d'in ma hakan ya faru ne a d'akin uwata mahaifiya." Yanda suke kallon juna kai kace basa gane yaren junansu, cikin mamakin dake son kasheta tace "Wa kenen? Ka fad'a min kaina ya kulla na gaza tuna komai." Marairaicewa yayi yace "Wallahi Hajia tsautsayi ne da kuma k'addara, ban shirya yin hakan ba, banyi niyyar yin hakan ba kawai aikatawa nayi." Fahimta da tayi yasa ta kafeshi da ido tace "Hamna ko Amna?" Saida yayi k'asa da idonshi yace *"Hamna."* "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un! Hasbunallahu wa ni'imal wakil." Wani irin kallo ta masa taja baya sosai tace "Wallahi Ammar ba dan kana d'aya d'aga cikin wanda suka min sanin shanu ba da yau saika raina kanka." Sunkuyar da kai yayi baice komai ba, d'auke kanta tayi daga gareshi tace "Jikana da jikanyata? A cikin gidana suka aikata zina? La'ilaha illallah." Jujjuya kai ta dinga yi tana ta fafutakar saita nutsuwarta, kallonshi tayi ta mik'e tsaye da duka sauran k'arfin daya rage mata ta gaura masa mari a kumatun dama tace "Kasan kayi wannan ta'asar akan me ka yarda aka aura maka yer uwarta? Kai wane irin shaid'ani ne Ammar, kayi tarayya da babba kuma kayi da gaba d'aya tazarar lokacin dake tsakaninsu bata wuce minti biyu zuwa uku ba." Komawa tayi ta zauna kan gadon ta kalleshi cike da jin haushi tace "Fitar min a d'aki." Mik'ewa yayi ya kalleta yace "Kuyi hakuri Hajia, wannan shine dalilin da yasa duk wanda yayi katob'ararsa yake rufe abarsa, kowa yafi so kiji daga baya yanda zuciyarki zata buga ki mutu kowa ma ya huta." Da kallo ta bishi, shima hushi ne yayi shiyasa ya fad'i haka, gajeran tunani tayi sai gata babu buk'atar yin zafi a wannan lokacin, kuma abinda ya fad'a gaskiya ne kawai, cikin taushin murya tace "Dawo nan Ammar." Tsayawa yayi daga shirin bud'a d'akin ya dawo ya zauna inda ta nuna masa. Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi ta rik'e hab'a tace "Duk laifina ne da bana iya fahimtar komai, kamata yayi ace na gane yarinyar dake gabana, amma ban gane hakan ba." Kallonshi tayi tace "Amma me yasa baka fad'a min har ka bari ka auri yer uwarta kuma? Ai da sai ka auri ita Hamna." Kallonta yayi shima yace "Ummy ce matsalar, bata so kowa ya sani sannan ta daina kulani." Cikin raha tace "Rabu da ita kawai, yanzu ma karka fad'a mata na sani nasan dai duk nice take jin tsoron kar na sani." Rik'o hannayenta yayi yace "Dan Allah Hajia ku gafarce ni ku yafe min, Allah nima ina jin kunyar kaina dan nasan ban aikata daidai ba, ku yanke min duk hukuncin daya dace dani zan d'auka, ba zan ji kunya ko tsoro ba, kuma zan nemi kowa yafiya daga iyayenmu dana zubarwa da mutumci har ita Hamna da kuma Amna." Da sauri ta girgiza masa kai tace "A'a Ammar, muyi shiru d'in shi yafi, ka sani a rayuwa akwai abubuwan da ba'a buk'atar su fito fili, yin shirun shine maslaha a yanzu duk da dai nasan akwai ranar da zasu fito, domin kuwa daga yanda yanzu naji sirrin k'uruciyata a wajenka ya tabbatar min babu wani abu fa da za'a b'oye bai fito fili ba, sai dai kafin mu fitar dashi mu fara duba maslahar dake cikin rashin fad'an da kuma fad'an." Cikin nutsuwa tace masa "Misali yanzu idan Hazida taji me kake tunanin zatayi?" Saida ya d'an rarraba ido yace "Ba zata ji dad'i ba Hajia." Da hannu ta masa alamar tace "Ba iya rashin jin dad'i kawai ba, hatta zumuncin dake tsakaninta da mahaifiyarku zai lalace, 'yarta ce fa data haifa kuma su kad'ai gareta, sannan ni kaina zata min alawadai da salon rainon nawa tace shiyasa ban barta da yaranta ba, shin zakaji dad'i idan haka ta faru?" Girgiza kai yayi a hankali yana d'an shigar da leb'enshi na k'asa cikin baki, d'orawa tayi da " Sannan ka duba al'amarin ta b'angaren yer uwarta da kake aure, Ammar ya zakayi ka fahimtar da ita sanda taji? Wane irin gamsashen bayani zaka mata?" Shiru yayi yana d'an girgiza kai, shi fa bai tab'a tunanin yanda Amna zatayi ba idan taji, kawai a yanda ya tsara ko da abin ya fito kowa yaji zai murje ido ne ya tsula tsiyarshi dole kowa ya shafa mishi lafiya, Amna kuma daya bubburma mata ashar tare da mahaukacin mari dole ko mafarkin yi mishi iskanci tayi sai tayi addu'ar tsari ta juya kwancinta, kamar Hajia tasan me yake tunani sai kuwa tace "Kasan adadin kishin matarka? Ammar kasan suffar da mace ke zama yayin data rikid'e sakamakon kishi? To ko da wasa ne ka jaraba ka gani, wannan mai tsoron na ka kamar mutuwarta zata kalleka ido cikin ido, rawar muryar da take sanda take magana da kai zata rera maka b'acin ranta kamar tana rera k'ira'a, shiru da takeyi sanda ka daketa to ba fa lallai ta iya yin shirun ba, Ammar, a wannan fannin ba lallai ka samu girmamawa daga wajen Amna ba, dan haka shirun nan shi yafi kamar yanda mahaifiyarka tayi." Cikin marairaicewa yace "Hajia to dan Allah ki yafe min, idan kika yafe min nasan komai zai zo min da sauk'i insha Allahu." Murmushi ta masa tace "Ba komai Ammar na yafe maka, nima ku yafe min kaji." "Baki mana komai ba Hajiata." Ya fad'a da murmushi, kallon agogo yayi da sauri ya mik'e tsaye yace "Hajia zan tafi asibiti yanzu, saina dawo." Kai ta jinjina alamar to, tana binshi da kallo har ya fita, yana rufe k'ofar d'akin ya sauke wata ajiyar zuciya mai k'arfin gaske yayin da yaji wani sanyi ya ratsa shi, ita kanta yana fita wani sakayau taji kamar ta rage nauyin wasu kaya data jima tana dakonsu a kanta. A falon dai ya same su dukansu, saida yaje kusanta ya kalli fuskarta, murmushi kawai yayi yana mamakin taya wannan innocent face d'in zata tabka rashin mutumcin da Hajia ta zayyana masa idan idonta suka rufe akan kishi, yo shi kwarjininshi ma zai barta tayi? Ganin ya tsaya kanta yana murmushi yasa tace "Yah Ammar ya dai?" Kallonta yayi sai kawai ya had'e girar sama da k'asa ya zama boss ya sunkuya yace "Kalli ido na." Bud'a matsakaitan idonta tayi ta kalli k'wayar idonshi, Hamna ma dake gefe tana jin ya fad'i haka ta kalle shi duk da ba ita yake kallo ba, tab'e baki tayi ganin sun k'urawa juna ido. Tana kallon idon nashi tayi saurin sunkuyar da na ta tana dariya tace "Ba zan iya ba yah Ammar, mutuwa zanyi da tsoron abinda nake gani." Wani shak'iyin murmushi ya mata ya shafa kumatunta yace "Ki ci gaba da kasancewa haka to ko da ranki ya b'ace a kaina." Sumbatar bakinta yayi yace "Ina sonki aljannata." "Nima haka." Ta fad'a tana mayar masa da martani, ta gefen ido ta harareshi ko da taji ya fad'i kalmar, tsaki tayi wanda yasa ya kalleta yace "Yarinya kiyi aure ki rage zafin zuciyar nan, kin ganni nan ba zan fasa abinda nayi niyyar yi ba da duniyata, wannan kayan halak d'ina ne kuma malak, naga wanda ya isa ya hanani yin abinda naga dama." A hassale ta kalleshi tace "To ina ruwana, dama na fad'a maka zan hanaka wani abu ne? Su dake halak d'in naka dai kaji da su, wasu ai sun maka nisa." Cike da rainin wayo yace "To ina ruwana dana wasu dama? Na ga dai duk abinda ke akwai can shine anan, to miye na k'aryar kuma?" Ita ma murmushi tayi tace "Banyi musu ba cewa akwai hallitu dayawa da suke iri d'aya da na ta ba, amma bai zama lallai komai ya zama d'aya ba, kamar yanda tasirin ma ba d'aya bane." Kallonta yayi da wata fassara a fuskarshi kafin ya kalli Amna yace "Duniyata na tambayeki mana? Yanzu dan Allah sai muka je shago tare muka siyo alawa iri d'aya a ledarta, yanzu zaki yarda na ce tawa tafi taki kyau da dad'i ko kuma ni na yarda idan kika fad'a min haka?" A tare Hamna da Amna suka ce "Ya danganta." "Ya danganta." Kallon kowace yayi sai Hamna data d'ora da cewa "Ya danganta idan ya zamana ita ta fika jin dad'in abu a bakinta, ko kuma ya zamana dama ta fika son alawar ko kuma ta fika sanin dad'inta, sannan zai iya yiwuwa a lokacin bakinta na da d'and'ano kai kuma naka baya da, ko kuma ya zama wunya take ji wanda hakan zaisa duk abinda ya shiga bakinta ta fika jin armashinshi, dole ko iri d'aya ce wani sai yafi wani jin dad'insa a baki, sann..." "Ke dallah can ya isa." Ya daka mata tsawa, hararanta yayi yace "Sai wani maganar jin dad'i da d'and'ano kike, amma dai kin yarda alawar d'aya ce ko? To Alhamdulillah daya zamana komai iri d'aya ne babu wata burga da za'a mana." Kallon Amna yayi "Yar banza shine kika shigar mata dan tana yer uwarki ko? Ke baki san bayan miji ake shiga ba." Lab'e fuska tayi dan haka ya kalli Hamna yace "Ke rumbud'ed'iya biyo ni na baki sak'o ki kawo ma masoyiyata." Kallon juna sukayi a tare, dan haka ya kalli Amna yace "Sak'on soyayya ne zan bata ta kawo miki." Da sauri cikin jin dad'i Amna ta kalleta tace "Dan Allah yer uwa tashi kije." Juyawa yayi zai fita Hamna tace "An k'i a je d'in, Allah Amna ki fita idona, kai kuma wallahi ka da ka sake tanka min k'ibata, idon sha'awarta kake kasa matarka tayi maka can ka cinyeta idan kana so, maye kawai." Yanda ta k'arashe da murgud'a baki da harara yasa shi kallonta yace "Ai aljannata idan tayi k'iba saita hanani fita gaba d'aya, a yanzun ya muka k'are tana neman kasheni bare ta k'ara auki." Wani haushi ne taji na neman kasheta, to wai akan me yake mata wannan rashin mutumcin? Ina ruwanta dashi ma da zai rik'a b'ata mata rai? Cikin shagwab'a Amna ta kalleshi tace "Duniyata, ya isa haka mana ka tafiyarka saika dawo." Kallon Hamna yayi yace "Kin ci albarkacinta, yanzu tashi muje na fad'a miki abinda nayi niyyar fad'awa masoyiyata." Cike da tsiwa tace "Ba zanje malam ka d'aukeni in ana dole." Bushewa yayi da dariya yace "Na d'aukeki? A gaskiya yanzu ban shirya ganin likitan k'ashi ba, gashi kuma yanzu rob ya k'ara tsada a kowane shago, dan haka ba zan iya ba amma wallahi sai kin je." "To na gani idan akai zaka d'auke ni." Nufowa yayi wajenta da sauri ta mik'e tsaye tana ja baya tace "Ammar bana son iskanci fa, Allah ka addabeni, wai kai baka da abunyi ne daya wuce ka bini a guje?" Kallonta Amna tayi ta kalleshi tace "Dan Allah yah Ammar ku fita farfajiya, ni dai kaga ba iya tashi zanyi ba bana so ku fad'o min ku k'arasani." Kallon Hamna yayi yace "Ni ne Ammar kai tsaye ko kankana? Kuma ni ne baki san iskanci? To ki rubuta wannan kalaman ki aje saboda ki iya tuna dalilin da yasa na hukuntaki yayin da na miki rugu-rugu." Hanya ya kama zai fita ya kalleta yace "Ke dai kinfi kowa sanin kalar nawa horon, tarihi nake kafawa mutum idan har na tashi zuwar masa." Gabanta taji ya shiga fad'uwa dakan uku uku da sauri, ai kuwa ta sani dan ya kafa mata wannan tarihin, to miye abunyi? Hak'uri! Na bashi hak'uri kawai tunda na ga jarababbe ne na k'arshe kuma kaifi d'aya, bugu da k'ari kuma bugu d'aya yake yi sak'onsa ya isa inda ya aika shi, kallon Amna tayi tace "Ina zuwa." Da gudu ta fita ta nufi wajen ajiya motoci, tana hangoshi ta tsaya tafiya d'aya bayan d'aya, har ya shiga ya tayar ya hangeta saiya bud'e ya zuro k'afa d'aya yana kallonta har ta k'araso, murmushin gefen labb'a yayi yace "Kin zo bayar da hak'uri ne? Munafuka kinji tsoro kenan?" Had'e fuska tayi ta harareshi tace "Allah ya sawak'e na baka hak'uri, kawai na zo fad'a maka..." Shiru tayi ta rasa abinda zata fad'a sai shi yace "Me kika zo fad'a min?" "Na zo karb'an sak'on ne." Ta fad'a da sauri, wani murmushin ya sake yi ya kalleta da kyau yace "Kankana, wannan kayan da kika ce sun min nisa ki sani daga yau su ma *mallakina ne*, ka da ki kuskura ki jawa wani tsautsayi ko k'arar kwana ta hanyar k'ok'arin mallaka masa mallaki na, in kuma ba haka ba to ki sani har ke sai nayi kasonki (prison)." Yana gama fad'a ya rufe murfin motar da k'arfi yayi baya baya ya daidaita ya fita a gidan, fitsari ne ko kuma ruwan haihuwa? Bata san ainihin meye ke son zubo mata ba tsabar kad'awar da cikinta yayi, to me yake nufi? Zai ajiyeta ne a haka yayi ta kallonta yana tsokanarta yana binta da gudu? Ko kuma karuwarsa yake da niyyar mayar da ita? Wannan al'amari yafi k'arfin tunaninta, amma zata k'aryatashi ta nuna masa ita ke da kanta bashi ba, zata nuna masa abinda ya faru ma ya k'wata ne da k'arfi ba da son ran ta ba ya karb'a, yanzu kuma zata bawa wanda ya dace ne, amma ba zata zauna ba kamar yanda yake mata wannan fatan, dan kuwa fatan zama ne yake mata. *Da dare* yana kan hanyarshi ta dawowa gida tsautsayi da ba'a saka masa rana ya afka mishi, mai mashin da wata mota ne suka kwatse sai kawai suka bigi tashi motar daga k'ofar da yake zaune, Allah ya kiyayeshi bai ji wani ciwo ba sai buguwa da k'afarta tayi, bayan jami'ai sun zo sunyi dube dubensu da aune aune aka tafi asibiti, ya so tafiyarshi gida amma lura da wani jami'i yayi yana d'an taka k'afarshi da k'yar yasa suka matsa mishi suka tafi, kafin a duba shi k'afar tayi sumtum bata takuwa, saida ya kalli mai motar d'aya wanda duk ciki shine baida gaskiya yace "Kai dai Allah ya saka min wallahi." D'aya daga cikin jami'an ne yayi dariya sai mai motar dake zazzare ido yace "Ayi hak'uri yallab'ai, tsautsayi ne." "Na gidan uban wa? Karka wani d'orawa tsautsayi kaji, ganganci ne da hauka." Duk yayi maganar ne yana danna wayarshi, Jibril ya kira dan a lokacin yasan shine ke da k'arancin abunyi, yana d'aukar wayar ya kara a kunne yace "Ka zo *Clinik katsina* ka same ni." Jibril ne yace "Katsina kuma? Me kake..." Bai barshi ya fad'a ba kawai ya datse kiran, juya akalar motarshi kawai yayi ya d'auki hanyar, bai d'auki lokaci ba ya isa can, tun a k'ofar asibitin ya ga motarshi, hankalinshi ne ya tashi ganin yanda murfin dake b'angaren mazaunin yayi, yana cikin kallo da mamaki yana shiga asibitin wayarshi ta sake k'ara, d'auka yayi inda mahaifinshi yace ya zo gida ya same shi, a cewar Jibril "To Abba ina zuwa, yanzu haka ma ina asibiti ne Ammar ya kirani." "Asibiti kuma? Wace asibitin ta su?" Cikin rashin tabbas yace "A'a Abba, ina ga fa hatsari yayi, dan ga motarshi can a waje ta bugu sosai daga wajen zaman matuk'i, amma dai bari na shiga ciki na gani." Cikin tashin hankali shima yace "Subhanallah, Ammar d'in?" "Abba ina zuwa." Ya fad'a yana kashe wayar ganin Ammar da yayi zaune jami'ai biyu tsaye a kansu, yana zuwa yace "Subahanallah, Ammar hatsari kayi?" Mik'a masa hannunshi yayi yace "Ba surutu nake so, muje kawai ka kaini wajen duniyata, baiwar Allah yau saura kad'an wannan hamagon ya kashe mata ni." Wani galala mutumin ya kalleshi, shima kallonshi yayi yace "Eh na fad'a, kayi hak'uri in zakayi in kuma ba zakayi ba ka mutu, ba zan iya b'oyewa bane har na tafi da magana a bakina kuma wacce ta shafeka." Kallon jami'an yayi yace "Sai anjimanku." Kamashi Jibril yayi sun fara tafiya kuma ya fizge hannunshi yace "Kai sakar min hannu bana so, dama dan jami'an su gane ya bigeni ne sosai ko sun ci tararshi dayawa, d'an banza ya ban haushi wallahi." Jibril kam kecewa yayi da dariya yace "Sharri kamar mace." Hararanshi yayi yace "Idan ba mace ce bani ai na mata ne, mace ta haifeni, mace ta haifi uba na da uwata, mace ce mahutata kuma insha Allahu a yaran da zan haifa akwai mace, to meya rage min kuma?" Jinjina kai yayi yace "Na ga ranar da bakinka zai rufe." Ba tare daya kalleshi ba yace "Sai ranar da k'asa ta rufe min ido." Da suka fita saida ya jira makanikenshi ya zo ya d'auki motarshi sannan suka d'auki hanyar gida. Labaran na jin Jibril ya katse kiran saiya kira lieutenant, shima yana d'auka abinda ya fad'a masa kenan, cikin tashin hankali ya kira Ummy dan yaji ko tana asibiti, cikin rashin fahimtar tambayarshi tace "A'a, lafiya meya faru? Ko jikin Hajia ne?" Cikin tashin hankali yace "A'a ba Hajia bace, wai Ammar ne yayi hatsari, Jibril yaje ya duba asibiti." Ummy dake tattara kayanta tana sawa cikin jaka zata tafi gida tana jin haka ta saki jakar tace "Me? Ammar? To ya yake dan Allah? Yaji ciwo ne?" Lieutenant ne yace "Ban sani ba nima." Cikin d'aga murya tace "To ka kira ka tambaya mana kaji, ya zaka ce min baka sani ba." Kashe wayar tayi da gudu gudu duk da goyon Shureim a gabanta haka ta fita ta shiga mota, a kid'ime ta zo gida ko zaman motar bata gyara ba ta fito da sauri ta shigo falon, a lokacin ba kowa ke falon ba daga Hamna sai kuma sauran yara da Zeituna Soueiba da Husseina, yanda suka ga ta shigo a firgice yasa Hamna kallonta tace "Ummy sannu da zuwa, lafiya dai?" Kusan saida ta kalli kowa cikin rud'u tace "Ammar basu zo ba?" Soueiba ce tace "A'a bai shigo ba, wani abu ne ya faru dashi?" Kamar zata fashe da kuka tace "Eh, ance yayi hatsari a hanya, kuma babu wanda yasan halin da yake ciki har yanzu." Da k'arfi ta mik'e tsaye kamar girgizar k'asa ce ta d'aga ta sama, dafe take da k'irjinta da taji kamar zai tsage zuciyarta ta fito, take taji hawaye sun kawo a idonta, cikin yanayin dake nuna damuwa da mai mahimmanci a rayuwarka tace "Ummy wace asibiti yake? Bai kamata mu zauna haka ba muna jiran tsammani." Kallonta duk sukayi, anya kuwa! To ai ba zaune suke ba da zata fad'i haka, Ummy ce tace "Ban sani ba nima Hamna, kuma yanzu daga asibiti nake ba can suka je ba." Karaf ta fizgi makullin motar Ummy ta nufi k'ofa tana fad'in "Zan duba duk asibitin dake garin nan." Bayanta Ummy tabi da sauri haka ma Zeituna, suna fita daga farfajiyar motarsu ta shigo gidan, tsayawa duka sukayi suna kallonsu, anan Jibril ya tsaya Ammar ya fito yana rintse ido da takawa da k'yar, tana ganinshi ta taka da sauri tana dudduba jikinshi, k'ura mata ido yayi yana kallo saida ta gama dubawa ta d'ago suka had'a ido, hannu tasa ta share yar k'wallar data taho mata ta kalleshi tace "Kana lafiya?" Saida ya d'an sunkuyo da kanshi kusanta yace "Kankana duk damuwa ne a kaina ta saki zubar da hawaye?" Kallonshi tayi sai taji haushin kanta da kunyar kanta sun kamata, saida ta d'an kalli gefenta taga Jibril ya sakar mata ido yana kallo, bata yarda ta juya ta kalli su Ummy ba kawai ta ruga a guje tayi b'angaren Amna, saida ta b'acewa ganinshi sannan ya kalli gabanshi, ido cikin ido suka kalli juna shi da Ummy, ga damuwa da tashin hankali da kuma soyayyarshi fal idonta, amma ba zata iya matsowa inda yake ba, Zeituna ce ta matso tace "Yah Ammar ya jikin? Hatsari kukayi?" Murmushi ya mata yace "Uwata karki damu kinji, ba wani babban abu bane ai, k'afata ce kawai ta d'an bugu, gashi ma da kaina na zo gida." "Allah ya k'ara kiyayewa to." Murmushi ya mata yace "Nagode, zan shiga ciki." B'angarensu ya nufa shima, su Zeituna na komawa suka fad'a ma su Husseina, nan suka fito suka nufi nasu b'angaren, yana shiga Amna na zaune kan kujera tana kallon Hamna data shigo mata a gigice ta ganshi yana d'angyasawa, da sauri ta taso tana fad'in "Duniyata lafiya? Meya sameka?" Rumgumeta yayi jikinshi wanda hakan yasa ya kalli Hamna dake bayansu zaune, murmushi ya mata inda yace "Kwantar da hankalinki me ni, d'an k'aramin ciwo ne karki sa min kanki a damuwa, ina lafiya." Ganin su Husseina sun shigo yasa ta raba kanta dashi ta taimaka mishi ya zauna, suma zaune sukayi inda suke jajata mishi suna tambayar ba'asi, nan ma wani zagin ya dinga zunduma ma mai motar nan su kam banda dariya babu abinda suke, sai Hamna dake kallonshi da mamakin irin halinshi, tana so ta tashi ta bar wurin amma ta rasa me yasa bata son yin nesa da wajen, Husseina ce tace ma Amna "Ki samu ruwan zafi saiki gasa masa k'afar, idan kin kamalla sai ki shafa masa rob ko victago." Mik'ewa Amna tayi kamar ba mai rumk'umemen ciki ba tana fad'in "To." Saida ta shiga madafa Hamna ta mik'e zata bi bayanta ta kalleshi tace "Ya kamata ka fad'a musu rob ya k'ara tsada, ina ga yanzu zaka buk'aci likitan k'ashin nan." Shigewa tayi su dai babu abinda suka gane, amma sai gani sukayi ya saki murmushi mai tsadar gaske, basu d'auki lokaci ba Amna ta fito ta nufi teburin abinci ta d'auko kwanuka ruwa da duk abun buk'ata, Hamna kuma na rik'e da roba d'auke da ruwan d'umi da k'aramin towel mai taushi sosai, a tare suka aje gabanshi sai Amna data shiga d'aki ta d'auko victago, cike da mugunta Hamna tace "Ban shi da kaina zan shafa mishi, yau zan gane k'aryar jarumtar da ake mana." Su Zeituna ta kalla tace "Aunty ku duba mana idonshi idan kuka ga alamar hawaye to akwai buk'atar ku fara d'inka masa atamfa." Rintse ido yayi, wannan magana ta k'arshe ba k'aramin tab'a shi tayi ba, shi Hamna zata ce a had'a da atamfa? Ma'ana fa ta mayar dashi d'an daudu, jar ubancen, shi kam da Hamna a matsayin matarsa take tayi wannan maganar daya mata luguden bulaliyarshi ko zata shiga hankalinta, dan ya fahimci duka ko zagi ba zai sata shakkarshi, tsayawa ya nuna mata mazantaka shine zaisa ta shiga hankalinta. Su Husseina dariya sukayi tare da tashi Zeituna na fad'in "Na yarda da jarumtar yah Ammar Hamna, ba zai bani kunya ba dan yana da uwa bafulatana, juriya da b'oye hawaye ba sabon abu bane ga fillo." Tana kallon cikin idonshi tace "Zamu gani." Husseina ma cewa tayi "Saida safenku." Kallonshi tayi tace "Ammarun Hajia yau fa gaka hannun 'yan biyun Ummynka, ya zata kasance gobe da safe kun bamu labari." Dariya akayi suka fice, Amna abinci ta zubo ta zauna kusa dashi ta dinga bashi a baki cikin kwanciyar hankali, jimawar da sukayi yasa Hamna cewa "Ke dallah kiyi sauri ki gama bashi sai kace zai cinye abincin shi na k'arshe." Kallonta tayi tana turo baki tace "Haba Hamna ke baki da imani ne, dubi fa yanda k'afarsa tayi ko motsi bayayi da kyau." Sunkuyar da kanta tayi hakan yasa shi tallabo fuskarta, hawaye ne suka kwaranyo wanda yasa shi jin tausayinta, tunani dayawa ne ya zo masa a daidai lokacin, yanzu fa irin wannan da ace akwai k'arar kwana da ya zatayi? Gashi tana da tsohon ciki daga yanzu zuwa kowane lokaci zata iya haihuwa, sannan akwai wata kulalliya tsakaninshi da yer uwarta da yake buk'atar ta yafe masa ko da bata san da al'amarin ba. Share mata hawayen yayi yace "Karki zubar min da hawayenki kinji, kada ki karya min zuciyata nima nayi kuka." Jinjina kai tayi tace "To na daina." Murmushi yayi yace "Yawwa to bani magani na nasha." D'aukowa tayi ta bashi yasha kafin ta kalli Hamna tace "Mik'o min ruwan." A daidai wannan lokacin sosai taji zafi zuciyarta, dan abun a bayyane yake cewa yar uwarta tafi iko da shi duk da ita ya fara sani, kuma bata da yanda zatayi daya wuce hak'uri, kasa tausar kanta tayi tana mik'a mata ta fice a d'akin da sauri har ta bar makullin motar Ummy anan, Amna bata kula da komai ba sai dai shi ya fahimci ranta bai mata dad'i ba, fuskar matarshi ya ci gaba da kallo tana gasa mishi k'afarshi wacce ke luf da bak'in gashi kwance kan jar fatarshi. *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘 *RAYUWAR RAYAM* 💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘 _*MY BK* INA TAYAKI MURNAR FARA SABON NOVEL D'IN KI, ALLAH YASA MU ANFANA DA DARASIN DAKE CIKI, ALLAH YASA YANDA KIKA FARA LAFIYA KI GAMA LAFIYA, ALLAH YA K'ARA MIKI LAFIYA MASOYIYA._ 🦯🚔🦯👮‍♀️ *KUTKALE*👮‍♀️🦯🚔 🦯 *(PRISON)* _MA SADIJA BARKA BARKA DA KAMMALA NOVEL D'INKI *KUTKALE*, ALLAH UBANGIJI YASA MU ANFANA DA DARASIN DAKE CIKI, ALLAH YA YAFE MIKI KURAKUREN DA KIKAYI A CIKI, ALLAH YA BAKI LADAR FADAK'ARWA, SAI MUN JIKI A NOVEL NA GABA INSHA ALLAH._ 🎂 *Sis Chappa*🎂 _Barka da k'arin shekara 3 a duniya, Allah ya karo shekaru masu albarka, Allah ya baki lafiyar anfanarsu ta hanyar data dace, bébé Khalid yace yana tayaki murna._ 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _51_ Ummy ta fito goye da Shureim zata tafi duba jikin Ammar Hajia ta fito daga d'akinta, tana ganinta tace "Ke kuma ina zaki je yanzu da dare da kika goya shi?" Cikin ladabi tace "Hajia zan duba Ammar ne." Da wani kallon rashin mutumci ta kalleta tace "Ban gane ba? Ammar d'in baya lafiya?" "Eh Hajia, d'azu ne ya samu hatsari a hanya, amma da sauk'i sosai k'afarsa ce kawai ta bugu." Cikin fad'a tace "Amma kuma shine banda darajar da wani zai shiga ya fad'a min halin da ake ciki." Tsaki tayi ta nufi hanyar fita waje, Ummy kuma tunaninta ko dai ta d'auka Amar aka ce shalelenta, dan haka tace "Kiyi hak'uri Hajia, dan naga ba kya jin dad'i ne shiyasa." Bata juyo tace komai ba sai ci gaba da tafiya da takeyi, ganin dai sun doshi b'angaren tare yasa Ummy cewa "Hajia Ammar ne fa." Cak ta tsaya ta juyo tana kallonta tace "Ammar ne fa? Eh Ammar d'in, me kike tunani? To saurara kiji da kyau, na jima ina rayuwa cikin k'arya da yaudara, jiya zuwa yau ne kad'ai nasan masoyana na gaskiya, duk gidan nan babu mai k'aunata kamar shi Ammar d'in." Juyawa tayi ta shiga ita ma tana biye da ita, babu sallama ta shiga ta samu Amna ta gama gasa masa k'afarsa, zaune tayi kan kujera kusa dashi tana kallon k'afarsa tace "Mijin ya jikin? Ashe takaba ka kusa sani, kaji yanda zuciyata ta buga, kada ka sake min irin haka gaskiya." Yanda ta gama maganar da shagwab'a, dariya sukayi sai Ummy data saki baki tana kallon, me ya samu Hajia ne? Ammar ne fa ko ta manta? Yaushe haka ta fara faruwa? Cikin murmushi Ammar ya ja hancinta yana rera mata baitin wak'ar gari ya waye yace "Haba, na gwadaki ne kawai dan ramawa." Cikin turo baki tace "Kuma duk gidan nan babu wanda ya iya fad'a min ma sai yanzu na sani." Saida ya saci kallon Ummy sannan ya kalli Hajia yace "Ai Hajia sai munsha lahaula, dan soyayyata dake yanda zata jijjiga wasu zaisa a kafa mana na mujiya, dan tunaninsu yaushe ne kuma tayaya haka ta fara faruwa." Wani kallo Ummy ta masa jin ya karanta mata tunaninta, dariya Hajia tayi ta mik'e tana dafe k'afarshi tace "Zan tafi saida safe zan zo muyi hira." Murmushi yayi har ta juya zata tafi sai kuma ta juyo, ba zato ba tsammani ta rarumeshi ta rumgume tana fad'in "Nima na rama buru-ubar da kake min." Sakinta tayi ta juya shi kuma yace "Ramuwa mai citta." Fita tayi Ummy na kallo al'ajabi duk ya kasheta, kallonta yayi yace "Ummy zauna mana, kawo min shi dan Allah." Ya fad'a yana tara hannu ta bashi Shureim. Kujerar da tayi niyyar zama ta kalla sai taga makullin motar ta, takawa tayi ta d'auki makullin ta nuna masa tace "Dama shi na zo d'auka." Juyawa tayi ta fita suka bita da kallo, murmushi kawai yayi ya mayar da hankalinsa kan Amna dake d'an ciccije leb'e, cikin kulawa yace "Lafiya dai?" Cikin yamutsa fuska tace "Ciwo nake ji yah Ammar, bayana ke wani irin abu ba dad'i." Cikin son gano abinda ke faruwa yace "Tashi ki d'anyi tafiya to ko haihuwa ce zata zo da sauk'i insha Allah." Had'e labb'enta tayi ta yunk'ura ta tashi, rik'e take da bayanta tana ta safa da marwa a tsakiyar d'akin, ikon Allah da yake haihuwar na kusa bata jima da fara wannan sassarfa ba taji ciwo na tasowa sama, kallonta yake duk inda tayi yana lura da halin da take ciki da kuma yanayinta, da fari duk sanda wuyan k'aramar rigarta ya fad'i saita jashi sama ta mayar, amma yanzu yaga bata kula ba har rabin k'irjinta duk a fili, ga kuma wata uwar zufa dake ta tsatsafo mata a goshi da wuya, sannan idan ciwon ya turnuk'ota saita rabka sallalami da dafe duk abinda ke kusa da ita ko ta durk'ushe k'asa, yanzun ma durk'ushe tayi amma kuma tashin ya gagara, hannunta ta d'ora kan k'aramin teburin dake wurin ta rintse ido sosai take fad'in "La'ilaha ilallah, ya hayyu ya k'ayyum bi-rahmatika astagisu, la'ilaha..." Da k'arfi ta kalleshi tace "Dan Allah ka kaini asibiti karna mutu, yah Ammar ka taimaka min mutuwa zanyi." Da sauri ya taso yana taka k'afarshi da k'yar ya durk'usa kusanta shima yace "Kalleni Amna, kalli fuskata kinji." Kai ta dinga girgizawa cikin rad'ad'i tana fad'in "Ba zan iya ba, ka kaini asibiti dan Allah, ka kira min Ummy, bayana ciwo yake kamar zai tsage." Mik'ewa yayi tsaye ya dawo kan kujerar da yake ya d'auki makullin mota da wayarshi, dawowa yayi kusanta ya tallabota da nufin su fita, tana mik'ewa sai kuwa ta cakumo rigarshi tamau ta fasa ihun data shiga dodon kunnenshi, yanda yaga tana neman sulalewa k'asa yasa shi azamar tarota, ya fara takawa da ita sai yaji tayi wani irin nishi kamar dai wani abu ya tunkaro zai fito, tsayawa yayi ya kalleta da kyau sai yaga daga inda take durk'ushe har inda suke yanzu duk wasu ruwa ne suka b'ata wurin, dafe goshinshi yayi yace "Oh mon Dieu." Da sauri ya fara latsa wayarshi ya danna kiran wayar Ummy, tunda taga kiranshi a wannan lokacin tasa a ranta cewa Amna ce ba lafiya, dan haka ma saida ta mik'e da sauri ta rarumi gyalenta kafin ta tashi lieutenant, tana d'aukar wayar yace "Ummy Amna ba lafiya, kiyi sauri ki zo." "To gani nan." Ta fad'a ita ma da sauri, tare da lieutenant suka fito yana rik'e da Shureim, fita tayi shi kuma ya je d'akin Hajia ya sanar da ita, tare suka k'arasa a lokacin Ummy na shiga Ammar yace "Ummy haihuwarta kusa take, ki dubata in zaiyi mu kaita asibiti." Kamata tayi ta kalleshi tace "Taimaka min da safa." Ya juya da niyyar shiga d'aki Amna ta sake wani nishi mai k'arfin gaske tana rirrik'e da hannun Ummy, haba mantawa yayi da ciwon k'afarsa ya juyo da gudu, yana zuwa makullanshi ya cillawa Ummy yace "Ummy bud'e min d'akin magani na." Da sauri ta mik'e ta shiga gaba shi kuma kamar wata yar beby haka ya lailayeta da iya k'arfinshi ya bi bayan Ummy, suna shiga da ita d'akin ya kwantar da ita kan gadon dake wurin musamman na haihuwa, Ummy kuma safa ta sanya da sauri ta tunkarota zata duba ta, kafin ta ida k'arasawa kusanta ta sake d'an d'agowa ta danno wani nishin kamar dai wanda take yi, haba ai wani abu taji ya zubo kamar kayan cikinta tare da wani irin gumi, kukan yaron da suka ji ne yasa Ammar saurin dawowa inda yaji kukan yaron ya sake bud'e k'afafun ta, bai tsaya saka safa ko wani abu ba kawai ya d'auki yaron da cibiya ta laulayeshi, cikin nutsuwa ya fara warware mishi da wani faffad'an murmushi a fuskarshi ganin yaronshi a hannunshi, Ummy ce ta matso tasa almakashi ta yanke cinbiyar, zata kai hannunta da niyar janyo uwa sai kawai Amna ta damk'i hannunta ta sake dank'aro wani nishin, fit sai ga wata santaleliyar budurwa ta fad'o ita ma sai wutsilniya take da kuka a hankali, kallon fuskar Amna yayi yace "Ke duniyata, ya kike neman kashe ni da farin ciki, daga farawa saiki fara min da bibbiyu." Kallon Ummy yayi baki bud'e yace "Ummy biyu ne, wallahi yan biyu ne, wayyo Allahna dad'i, Amna nagode nagode kinji, Allah ya saka miki da alkairi." Lumshe ido Amna tayi ta kwanta luf, Ummy ce ta kalleshi tace "Ka d'auko mana kayan haihuwarta." "To Ummy." Ya fad'a yana nufa k'ofa rik'e da jinjirin, kallonshi Ummy tayi tace "Ina kuma zaka je dashi a haka?" "Oh." Ya fad'a yana dawowa ya mik'a mata shi, aje shi tayi gefen Amna ta yanke cibiya ta fito mata da uwa, hannu tasa ta fito mata da gudan jini, kallonta tayi tace "Amna ci gaba da tausa ciki kina murzawa saboda jini ya fito." Ido rufe tasa hannu tana murza ciki tana danna mararta tana ji jini na zubo mata. Yana fitowa ya ga duk iyayen tsaye Zeinabu ce kawai babu, cike da shak'iyanci ya fara taka rawa yana tafa hannaye yana juyawa, takon rawar a hankali mai birgewa, a haka kuma wak'a ya dinga rerawa ta godiya ga Allah wacce shi ya k'irk'ireta yanzun nan, lieutenant ko da yaga haka yasan ta haihu sai shima ya fara tapi yana biyar wak'ar yana gyad'a kai alamar yanayi da wak'ar sun masa dad'i, Hajia ce tace "Kai ta haihu ne?" Girgiza kafad'u ya shiga yi yana kallon fuskarta ya kwaso shoki daga k'ololuwar k'asa yayi sama da ita ya wurgata fuskar Hajia yana fad'in "Hajia 'yan biyu ta haifa min, aradu mace da namiji ne Hajia, kai nima fa ashe jarumi ne." Murmushi ta masa tace "Hakane, amma duk jarumtarka mijina dai ya fika, shi uku yake haifa." Alhaji dake tsaye rik'e da carbi kunya yaji ta kamasa, su lieutenant da Labaran kuma dariya sukayi cike da jin kunya, shafa kumatunta yayi yace "Bari na dawo Hajia Allah yau sai kin taka rawar jin dad'i." Da gudu kamar yaro ya nufi hanyar b'angarensu, da sauri ya d'auko kayan ya kawowa Ummy, Ummy da kanta ta gyara yaran ta bashi ya kawo musu, yana dawowa ya samu tana dannawa Amna mararta da jini ke ta fitowa, tana kallonshi tace "Zare nake so zan mata d'inki." Kallon Amna yayi ya matsa kusa da ita yace "Wayyo duniyata yarana sun k'ara ki ko, sannu kinji, insha Allahu ladar ta tabbata gareki." Rufe idonta tayi a ranta tace "Kai da kan ka ma ka k'ara ni bare su, ai kamar uba kamar 'ya'yansa ne." Da kanshi ya had'awa Ummy zaren ya bata kafin ta fito, namijin dake hannun lieutenant ya lek'a fuskarshi yana wasar masa baki yana fad'in "Kai wanene wannan? Kai yaron babanshi ne, d'an albarka ne, yaron Ammar ne wannan." 😂😂😂😂 *Allah ya kyauta.* Soueiba ce ta kalleshi galala tace "Ammar yaron da ko ido bai bud'e ba kake ma wasa?" Kallonta yayi yace "Ina so ya fara d'aukar sautin muryata ne kafin ta kowa." Tab'e baki Hajia tayi tace "Duk tsiyarka kuma sai sun sun gane uwarsu kafin kai." "Wannan ba matsala bane Hajia, ta cancanci haka ai, daga yanda naga ta canza d'in nan a yayin nak'udarsu na k'ara mik'o muku jinjinata." Kalle kalle ya shiga yi kafin yace "Wai duk ina sauran mutanen gidan." Husseina ce tace "Suna bacci mana, *12: 30* ce fa tayi na dare." Zaro ido yayi yace "Wa? Bacci a lokacin da yan biyu na suka shigo duniya, ai Qur'ani basu isa ba, duk uban daya tsaya ma mutum ma saiya tashi, bari kuga yanda zan firgita nutsuwar kowa." Labaran ne ya bishi da murmushi yace "Mun gode Allah da yasa ubannin gamu nan tsaye." Dariya lieutenant yayi ya kalleshi yace "Kar ya baka wahala mana." Suna kallonshi ya nufi wajen mai gadi kai tsaye ya fara bubbuga mishi k'ofa, yanda yaji buga k'ofar yasa shi fitowa da sauri da makullai a hannu yana tunanin fitar gaggawa ce, yana ganinshi ya tsaya yace "Alhaji k'arami wani ne ba lafiya? Bara a bud'e k'ofar." "Kai tsaya dallah." Ya fad'a yana turashi baya, kallonshi yayi zuru da ido kafin yace " Ina bokitin nan naka da kake wanki?" Saida ya had'e gira tsabar mamaki yace "Bokiti? Yana nan ciki?" "D'auko min." Ya fad'a, shiga ciki yayi ya d'auko bokitin robar ya kawo mishi yana fad'in "Yallab'ai lafiya dai ko? Allah yasa ba laifi nayi ba." Kallonshi yayi yace "Idan laifi kayi kuma shine sai a bokitinka zan huce saboda tsoronka nake ji." Sunkuyar da kai yayi shi kuma ya juya zai tafi sai kuma ya tsaya ya juyo yace "Baka da wani mabugi haka kamar sanda ko icce?" Shi kam mai gadi baya da dan ko shayi ko girki idan buk'atar yi ta kamashi k'aramin gas gare shi, dan haka yace "Babu yallab'ai, amma bari a samo maka." Takalminshi yasa da niyyar fita nema sai Ammar yaga tsumagiya aje, d'auka yayi yace "Bari wannan ma yayi." Juyowa yayi ya kalleshi yace "Yallab'ai da ka bari na samo maka wanda yafi wannan, ita ma ina ajiya ne saboda yara wani lokacin." Kallonshi yayi saida ya kawo bokitin nan gaf da kunnenshi ya tak'ark'are ya had'a tsumagiyar nan da bokiti ya shiga bubbugawa da k'arfi kamar zamanin da ake shela da baki, rintse ido yayi sosai saboda yanda k'arar ke shiga hudar kunnenshi, saida yaji yayi shiru sannan ya bud'e ido ya kalleshi, shima kallonshi yayi yace "Har gari ya waye babu mai kwana a gidan nan, baiwar Allah na can tasha fama ta haifo min yara har biyu, biyu fa." Ya fad'a yana nuna mishi biyu da yatsunshi ya ci gaba da cewa "A lokaci d'aya, kuma kuma ku kuna baccin iya shege." Juyawa yayi cikin takon k'arfi kamar zai shiga filin daga ya shiga falon Hajia, saida ya tsaya tsakiyar falon ya fara bubbuga bokitin yana ihu yana fad'in "Kowa ya fito, kowa ya tashi." Har sama ya haura k'ofar kowane d'aki ya bubbuga yana shelar kowa ya fito, har yara masu nauyin bacci saida suka fito haka Zeinabu da Hamna take hangenshi daga sama, Kamal ne ya iya jarumtar cewa "Yah Ammar lafiya ka tashemu a bacci?" Kallon duka yaran yayi yace "Kowa ya sauko k'asa." Cikin turo baki da girmama jarabarshi kowa ya sauko rai a b'ace, kamar zai basu horan yak'i haka suke jera suna kallonshi, kallonsu shima yake yace "So nake ku fita farfajiyar gida kuyi murna kuyi tsalle kuyi ihu da hauka saboda murnar samun 'yan biyu da nayi, yan biyun ma ni duka jinsin aka had'a aka ban, dan haka ina so duk unguwar nan ta shaida anyi sabon *Ammar* da kuma k'anwarsa *Amna*." Yanda ya fad'a haka suka fita duk sukayi inda suka ga su Hajia, d'aga kai yayi suka had'a ido, girgiza kai tayi a ranta tace "Allah ya shiryaka Ammar." A zahiri kuma ce masa tayi "Saboda wannan ne ka d'aga mana hankali? Allah ya baka lafiya to." Sake d'aga kai yayi yace "Ki sauko kema ko kuma na sauko dake yar bak'in ciki, hassada kike min na samu 'ya'ya biyu a lokaci d'aya." Wani murmushi ta masa tace "Biyu ko uku?" Dara daran idonshi ya sake kafewa kanta da mamaki yace "... *Alhamdulillah* *Wallahi rashin comment yasa duk rubutun ya fice min a rain, ba zan dakatar da rubutun ba amma zan iya daina turawa ko ina, idan kun canza na samu gamsuwa zaku ga wata page gobe insha Allah ba ma sai kun tambaya ba.* _A kafta, yawan sharhi yawan rubutu._ 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _52_ "Yan uku kankana?" Yawu ta had'e duk tayi alamar rashin gaskiya, ganin bai daina kallonta ba yasa ta juya zata koma d'akinta taji yace "Har d'akin zan sameki wallahi idan baki sauko ba." Juyowa tayi ta kalleshi, yamutsa fuska tayi ita kam ba zata iya wannan tozarcin ba, hararanshi tayi tace "Hijabi zan d'auko to, saboda gidan nan ba tsaro gareshi ba, ta ko ina kuraye ke akwai ko ganye suka gani kallon nama suke mishi." Da kallo kawai ya bita har ta fito, kallon saukowarta yake da dogon wando sai hijab daya rufe iya cinyarta, saita ta kawo daf da shi suka jera zasu fita yace "Duk kurar da take ma ganye kallon nama lallai lafiyayya ce, shiyasa fa har yanzu nake mamakin yanda akayi baki karb'i sak'on dana tura miki ba bayan kuma ina da tabbaci akan d'an aike na." Hararanshi tayi ta murgud'a baki tace "Ta Allah ba taka ba, burinka kenan a kaina kuma ba zai cika ba." Suna zuwa Ummy ta fito ta kalleshi tace "Malam muje dan Allah ka kaimu asibiti idan ka gama shiriritar." Turo baki yayi gaba ya kalli mutanen dake wurin yace "Yanzu jama'a ba zan iya samun wanda zai kira ni ya danganta yaran nan dani ba?" Alhaji ne yace "To uban..." Kallon yaran yayi yace "Da fari fad'a mana sunansu? Ko kuma ka bamu zab'i ne?" Da k'arfi tace "A'a Alhaji, haba dai kura da shan bugu gardi da kwashe kud'i, ai yanda nake ubansu haka zan saka musu suna." Hamna ce ta kalli Ummy tace "Ummy ina Amna?" Nuna mata d'akin tayi tace "Tana ciki." D'akin ta shiga dan ganin yar uwarta, shi kum saida ya gyara tsayuwa sannan yace "Namijin sunan *Ammar*, macen kuma domin nuna farin cikina ga uwarsu na mata takwara, dan haka ita ta ci *Amna*." Kallon kallo aka shiga yi harda yaran, lieutenant ne yace "Meye na mayar musu da sunanku to kamar suna ya k'are?" Murmushi yayi yace "Abba ai duka sunaye ne masu kyau, ina so jarumi na ya zama namiji marar tsoro da fargaba, ya zama babu shakka babu d'aga k'afa kuma zai iya fad'a ko a gaban waye, sannan ya zama wanda baya d'aukar raini, jarumata kuma zan so ta zamar ruwa masu aiki sannu kamar mahaifiyarta, hakan zaisa kowa ya so ta." Lieutenant ne yace "Idan na fahimce ka kana so ka saka mishi sunanka saboda kana so yayi komai naka ko?" "Eh Abba." Ya fad'a cike da kuri, jinjina kai yayi yace "Har da fitsarar da rashin ta idon ma?" Kwab'e fuska yayi alamar shagwab'a yace "Abba ni ne marar kunyar?" Murmushi lieutenant ya masa yace "A'a d'an albarka." Husseina ce tace "To wai akan me sai sunayenku za'a mayar ma da yaren kamar wad'anda suka mutu?" Alhaji ne yace "Dan Allah ku barshi tunda haka yake so ai ya hallata, kawai mu dai ya fad'a mana wani sunan ko da alkunya ce da zamu dinga kiransu dashi, d'an ba zamu kiraku da sunanku ba kuma suma mu kirasu da sunanku." Girgiza kai Hajia tayi ta kalleshi tace " *Shalele* na, fad'a mana alkunyarsu ko kuma na saka musu da kaina." Kallon kallo aka shiga yi Hajia ta kirashi shalelenta, basarwa kawai tayi shi kuma saida yayi tsayuwar tata rashin mutumci yace "Eh to shi jarumin Ammar d'in zaku iya mishi lak'abi da *Abu Ahmad*, sunan da zai sawa d'anshi kenan insha Allah, jatumar tawa kuma saiku mata lak'abi da *Ummu Aysha*, idan kuma alkunyarsu kuke so saiku kirasu da *Ameer* *Ameera*, idan kuma a sauk'ak'e kuke so saiku ce *A.A*, ita ma kuma saiku ce mata *A.A*." .Cike da k'aguwa Ummy tace "Ba zan iya sauraren wannan shirmen ba, yarinyar can asibiti take buk'ata a bata kulawar data dace, amma kun tsaya kuna maganar sunan yara tun yanzu." Juyawa tayi cikin jin haushi ta shiga ciki, Hamna ta samu rik'e da hannun Amna cikin sanyin murya take fad'in "Yer uwa wallahi ban tab'a tsammanin haka haihuwa take ba, ta zo min da sauk'i fiye da tunaninki, sannan yah Ammar ya tsaya kaina har na haihu, gaskiya naji dad'in kulawarsa a kaina." Murmushi Hamna ta mata tace "Yanzu ma gashi can sai hauka yake mana a gida wai shi yayi yara, ya hana kowa bacci fa." Murmushi tayi tace "Ba hauka bane yer uwa, farin ciki yake ya d'ora idonshi akan 'ya'yansa." Kamata Ummy tayi tana fad'in "A ganinki haka murna ce? Wannan ai hauka ne da shirme, kanshi aka fara haihuwa?" "Ummy a gareshi shine na farko." Cewar Amna, da sauri Ummy ta kalli Hamna ita ma kuma ita ta kalla, kamata sukayi ta tashi Ummy ta mata durwa (k'unzugu) sannan suka fito, sun same su tsaye sai zuba musu haukan ko yake ta bakinsu, sunaye kawai yake zana musu idan basu iya fad'in wannan su fad'i waccen, rankaya sukayi zasu fita ya kalli Hamna ya cilla mata makulin mota yace " Ke b'ukekiya tuk'asu ina zuwa." Hajia ce tace "Ina zaka je kuma?" Kallonta yayi yace "Ku dai ku tafi gani nan." Hamna da bak'in ciki ke neman kasheta tsabar haushi kawai taji hawaye sun taho mata, lieutenant ne yayi sauri matsowa kusanta yace "Ke lafiya? Meya miki?" Saida ta nuna Ammar tace "Abba na fad'a mishi bana so yana shammatar min jiki amma ya k'i dainawa, haka kawai kamar maye ya sa min ido." Kallonta yayi da mamaki yace "Ke ni banda lokacinki, girma ya zo min yanzu na wuce ajinki wallahi." Yana fad'a ya wuce b'angarensu, k'ofar Amar yaje kamar Allah ne ya aikoshi ya shiga jijjiga mishi k'ofa, cikin kasala ya taso ko baccin ma baiyi ba su gama tijara shi da Umaimah kan shinfid'ar gado da bata gyara masa ba, yana bud'ewa Ammar yace "Shege, wato ina can ina bud'ar baki dan murna ku kuna can kuna nanik'e tsakani k'ugu da k'irjin matanku, to fito kaje ka d'ora mana shayi a k'ofar gida zanje na tado sauran matsiyatan." Da mamaki Amar yace "Ammar Amna ta haihu ne?" Cike da isa yace "Biyu, biyu yaro ta haifa min, a halin da ake ciki yanzu zan iya bada 'ya kuma nima za'a iya bani 'ya." Wani mamakin ne ya sake lullub'e shi yace "Ban gane ba, kar dai yan biyu ta haifa maka mace da namiji?" Sororo ya kalleshi yace "Ban gane kar dai ba? Bai kamata bane ko me kake nufi?" Cike da damuwa yace "Kai sarkin masifa, ni ba haka nake nufi ba." Hanyar b'angaren Junaid ya nufa yana fad'in "To maza kaje ka d'ora mana shayi." Niyyar komawa ciki yayi yana fad'in "Ba uban da zan d'ora ma shayi yanzu ehe." Shi dai baisan ya akayi ba saiji kawai yayi har ya shak'o wuyan rigarshi yana fad'in "Sai ni Ammar, ni zaka d'ora ma inba haka ba ubanka zaka ci Allah a cikin daren nan." Cikin son k'wak'ule hannunshi yace "Naji to zan d'ora sake ni." Sakinshi yayi da sauri ya shige ciki yana fad'in "Sai naga tsiya yanzu in zaka biyo ni ciki ne." Saida ya rik'e k'ugu yace "Kai dai kafi kowa sanin waye d'an uwanka, kaine zaka bayar da labari na ba wai wani ya baka ba, k'arami ne a cikin k'ananun aikina na shiga ciki, to miye a ciki? Daga kai har Umaimah a gabana kuka girma, dukanku k'annai na ne to sai me." Juyowa Amar yayi ya mayar da k'ofar ya rufe ya tunkari inda yake jin k'arar motoci yana fad'in "Naji dan Allah zan d'ora, je taso sauran." A wurin Junaid ma haka abun yake bayan ya gama kiranshi gwauro sannan ya iza k'eyarshi gaba, Jibril ma haka taso shi gaba yayi har da Jamil ma bai bari a baya ba, yana dawowa k'ofar gida ya same su mai gadi na kunna musu wuta a mangal, Jibril ne yayi wata doguwar hamma yana fad'in "Allah gamu gareka, wannan lamari sai kace a mulkin mallaka." Junaid ne yace "Muyi fata kawai d'ora shayin nan ba kullum zai ce sai mun d'ora ba, dan in kullum ne akwai matsala wallahi." "Shawara mai kyau." Ammar ya fad'a daga bayansu, saida ya k'araso yace "Yanzu ku haihuwar da aka min ita ce ba zaku iya tayani farin ciki ba duk kuke k'ananan maganganu, sai yaran sun girma kuma kuce zaku dakesu wai sunyi ba daidai ba, to duk uban da bai tayani murna yanzu ba yace zai dakar min yara Allah shari'a ni dashi daga nan har tahatas-sara." Junaid ne yace "Allah ya baka hak'uri duniyar Amna, farin ciki mu ai mun fika dan mu aka ma haihuwa." Kallon jamil yayi yace "Jamalun (rak'umi😂, amma ya cuceka) shiga ciki ka samo k'atuwar tukunya da wake da shinkafa ka d'ora mana, zanje yanzu a samo mai yanda zai ishi kowa har ayi wanka dashi." Jamil take ya b'ata rai kamar zaiyi kuka, shi kuma meya had'ashi da dafa wake da babbar tukunya? A ransa yayi tsaki ya shige cikin gidan kamar ya kwamtsa ihu, kallonsu yayi su kuma yace "Kuyi da jiki mana kuna abu kamar yan mata." Amar ne ya kallesa a ransa yace "Yau ni naga ikon Allah, kuma ba damar magana wannan jaraba." Hannu ya tara musu yace "Mai makullin mota ya ban." Junaid da makullinshi ke tare dana d'aki ne ya mik'a mishi yace "Dan Allah yanda na baka motar nan lafiya ka dawo min da ita lafiya, kar kaje ka ja min jarfa ka sani zuwa ofishin yan sanda ko gendarmerie." Hararanshi yayi yace "Wato ga Ammar masifaffe jarababbe d'an masifa d'an bala'i wanda aka haifa ana tsaka da yak'in duniya na farko." K'wafa yayi ya shiga gidan Amar yace "To me ya rabaka da abinda ka fad'a d'in." Yana d'aukar motar ya fito da gudu da gangan yayi kansu hakan yasa su watsewa daga wurin a tsiyace, yana wucewa ya zuro kai ta k'ofa ya musu gwalo, kai dukansu suka girgiza, bai d'auki lokaci ba ya isa asibitin, ya samu Ummy da ma'aikaciyar dake aikin kwana a asibitin sun gama kimtsa Amna duk abinda take buk'ata sun mata tare da yaran, har an shiga da ita d'akin hutu ta kwanta tare da duka yaranta, su Hajia ne suka musu sallama suka tafi sai Husseina aka bari da Ummy su kwana anan, har Hamna zata shiga mota yace "Ki bari zamu tafi tare dake." A lokacin babu wanda ya iya tanka masa dan ba k'aramin shan kunu yayi ba, hatta Ummy sai taji tsoron ko da hararansa bare tace a'a, ita kanta Hamna ta tsorata sosai sai kawai ya shige ya barsu, ko da suka koma ciki Ummy ya tambaya abinda suke buk'ata, magunguna ta rubuta wanda zasu taimaka mata ya siyo ya dawo, lokacin sukayi saida safe suka fito shi da ita. Tunda suka d'auki hanya babu mai magana sai Hamna dake addua'r Allah ya kaisu lafiya, saida suka kusa kaiwa gida ya taka birki ya jingina bayanshi a kujera, kanshi na kallon sama kamar ba zaiyi magana, tunda taga haka ta fara sallalami da duk addua'r da ta zo bakinta, tana tsaka da addua'rta taji muryarshi irin babu wasa a ciki yace "D'azu kinyi maganar yara uku, me kike nufi da abinda kika fad'a?" Saida ta zaro ido tsabar tsoro kafin ta k'ank'ancesu a ranta tace "Yayin da wasu ke zuwa duniya lokacin wasu ke barinta, Hamna kuma ta wannan hanyar k'arshenki zai zo." Ba tare data kalleshi ba cikin b'ari da rawar murya tace "Ba..ba abinda na...ke nufi, ina tambayarka ne kawai." D'agowa yayi ya daki sitiyarin motar da k'arfi ya kalleta yace "Hamna na miki kama da sakarai ne?" Haba wane mutum, ai sai ta fashe da kukan da babu hawaye tana girgiza kai tace "A'a, a'a yah Ammar, dan Allah kayi hak'uri ka kaini gida." Cikin tsawa yace "Idona zaki kalla ki min magana." Da sauri ta kalli fuskarshi sai kuma tayi k'asa da kanta tace "Dan Allah kayi hak'uri karka cutar dani." Bayan wuyanta ya shak'o ya matso da fuskarta gaf dashi yace "Ni zaki rainawa wayo Hamna, tun a waccen lokacin naga alamun ciki a tare dake, kwanciyar hankalin Ummy kawai yasa nayi shiru, amma yau ba zan barki ba sai kin fad'a min gidan uban da kika kai min ciki na." Yanzu kam kuka ta fara na k'warai sosai har hawayen na shiga bakinta sun jik'e leb'enta sharkaf, ganin bata da niyyar magana yasa shi sakinta ya kuma dukan sitiyarin motar da k'arfi har wata razananniyar oda ta fito, k'amewa ta sakeyi ya kalleta cikin jin haushi yace " Hamna bana son dukanki, ke kad'ai ce bana jurar ganin cutuwarki, ki taimaka ki fad'a min ya kikayi da cikin nan Hamna, idan kuma kin zubar dashi ne kamar yanda nake tunani ki fad'a min." Kallonshi tayi cikin kuka jin ya fad'a mata mafitarta, sunkuyar da kai tayi tace "Kayi hak'uri yah Ammar." Lumshe ido yayi a k'alla tsawon minti biyar yana saita nutsuwarsa, saida ya daidaita kansa ya kalleta yace "Nayi hak'uri da me? Da cikin nawa da kika zubar?" Da sauri ta d'aga masa kai alamar eh, rintse ido yayi ya yamutse fuska kamar zaiyi kuka, ya d'an jima a haka kafin ya bud'e ido yana sauke ajiyar zuciya ya kalleta yace "Hamna kinsan me zai hana ni sake miki wani cikin a yanzun nan?" Fik'i-fik'i ta masa da ido ta kuma kallon titi ba tace komai ba, d'orawa yayi da cewa "Saboda yer uwarki ne, wallahi ba dan Amna ba da saina miki wani cikin naga abinda zai faru, ke ko da zaki zubar dashi ne saina k'ara miki wani sai dai mu tabbata a haka, amma..." Kallon titin shima yayi cikin nutsuwa ya ci gaba da cewa "Ina ganin mutumcinta sosai, ina girmama al'amarin Amna har zuciyata, ina ganin k'imarta da darajarta a idona, ta kasance wacce tafi kowa kusanci dani, ta zauna dani sanda kowa ke kirana mahaukaci da ganin rashin tarbiyata, ta zauna dani ta fahimce ni ta shanye komai daga gareni, ta juri dukana ta shanye bak'ar maganata tayi dariya ga fitsarata, duk sanda na zalinceta bata tab'a fitar da k'walla a idonta ba sai dai tayi kukan da babu hawaye, duk sanda nayi niyyar dukanta bata guduwa sai dai ta tsaya wurin ta shiga bani hak'uri, wannan haukan nata na birge matuk'a. Ki sani yau kinci albarkacin yer uwarki, ba dan haka ba da sai kin gane kurenki na zubar min da ciki da kikayi, amma ko yanzu ma zaki gane kuren naki." K'wafa yayi mai k'arfin gaske tare da tayar da motar ya fara ja, suna tafiya ya juya ya kalleta, ganin har yanzu bata saki jikinta ba sai share hawaye take, wani uban rank'washi ya gaura mata akai yana fad'in "Shegiya 'yar bak'in cikin tsiya, wai yaron ne da zaki haifo min kike jin haushi da hassada, a ganinki da ki haifo min shi gwara kin min asararshi, to Allah ya isa Allah saiya saka min wallahi dan ba yafe miki zanyi ba, mai bak'ar zuciya kawai." Tunda ya rank'washeta ta baje baki tana kuka, cikin jin haushi ya sake shirga mata k'ulli a baya yana fad'in "Dan ubanki rufe min baki, Allah kinci sa'a bana son dukanki da saina karya k'asusuwanki yau a garin nan." Hamna dai da yake muguwa ce k'ala ba tace masa saida suka isa gida tana wannan kuka kamar an mata mutuwa, a k'ofar gida ya tsayar da motar ya bud'a zai fito ita mata fito fuska rufe da hijabi, nufa yayi wajensu Junaid dake zaune suna hira suna aikin daya sa su, saida ta bud'e k'aramar k'ofa zata shiga dama wandon bacci ne gareta ta kalleshi tace "Ammar mugu Ammar azzalumi mai bak'ar zuciya, Allah ya isa Allah ya saka min duk cut..." Da gudun bala'i ta k'arasa shiga ciki kamar zaki ya biyota ta haye sama, Ammar daya bita da kallo su Amar ne suka kwashe da dariya, kallonsu yayi a k'ufule yace "In ban muku wanka da tafasashen shayin nan ba ku ce ba namiji bane ni." Kowa kama bakinshi yayi kamar sun cika iska, ture Jibril yayi daga kan kujerarshi ya fad'i k'asa ya zauna yana fad'in "Zan kama ki ne yarinya, Allah zaki san ni kika tab'o yar banza mai zubin gwiwar daji." Amar dake ta rik'e dariya ne ya kasa ya mik'e tsaye ya mik'o mishi d'an k'aramin bol d'in shayi na glas yace "Babban yaya ga shayinka, premier ( na farko) ne." Lokacin kowa ya samu damar sakin dariyarsa har da masu rik'e ciki, kallonsu yayi da niyyar masifa sai kuma ya fashe da dariya shima yasa hannu ya karb'a ya kurb'a, saida ya kallesu ya sumbaci yatsunshi biyu ya jefa musu sumbar yace "Ina sonku k'annai na, kune rayuwata fa." Jamil ne ya fito duk yayi gumi yana ganinshi yace "Yawwa Jamalun ya ake ciki? Waken ya dahu ne?" Cikin jin haushi Jamil yace "Da k'yar na tashi Nana daga bacci ta bud'e min madafa, da k'yar na samu na d'ora ruwan, yana can zata k'arasa dafawa." Girgiza kai kawai yayi suka ci gaba da zuk'ar shayinsu suna hira, wani abun daya fad'a kowa sai yaji abun wani iri, wani suyi dariya kamar cikinsu zai fashe wani kuma su girmama al'amarinshi, kamar yanda ya fad'a kam saida akayi sallah asuba kad'ai ya barsu suka koma cikin gida shima ya shiga ciki, wanka yayi ya canza kaya farare tas wanda rigar t-shirt ce sai wando 3 quater kafin yasha magani saboda k'afarsa da har ya manta akwai ciwo, kiran Ummy yayi ya tambayesu yanda suka tashi tare da neman a bashi Amna, sosai suka jima suna hira cikin nishad'i kafin suyi sallama yace sai ya zo d'aukarsu. Misalin *06:30* na safe Hamna ma ta kirasu suka gaisa ta tambayi yara, saida suka gama waya har ta kashe Amna mijinta ya zo tunaninta, tunawa tayi da fa ciwo a k'afarsa, sannan mutum ne dake wasa da cikinsa, idan ya ga abinci ne zai ci idan kuma bai gani ba babu ruwansa, ita kanta wani lokacin sai tayi rarrashi yake ci kafin ya fita da safe, sake kiran Hamna tasa Ummy tayi ta bata wayar, tana d'auka tace "Na'am Ummy." "Ni ce yer uwa." Ta fad'a murya k'asa k'asa, d'orawa tayi da "Dan Allah yer uwa wani taimako zaki min." Daga b'angarenta ta amsa da "Wane irin taimako kuma Amna? Kin fara manta yanda muke ne?" "A'a, amma nasan abu ne mai wuya a wajenki, ki min alk'awarin zaki min kafin na fad'a miki dan Allah." Cikin rashin son wasa tace "Fad'a min ina jinki, nayi alk'awarin." Cikin muryar rarrashi tace "Yer uwa taimaka min zakiyi dan Allah idan an kammala abin kari ki kaiwa yah Ammar, sannan idan kinje ki d'ora masa ruwan zafi ki ce masa ya gasa k'afarsa sosai sannan yasha magani, dan Allah." Ta k'arashe da sake kashe murya. Wani mamaki ne ya kashe Hamna tare da tunanin taya zata je su had'u bayan abinda ya faru jiya? Gashi kuma tayi alk'awari, bayan alk'awarin kuma tasan halin Amna da rik'o zata iya yin hushi da ita akan haka, a hankali ta bud'a baki tace "Shikenan naji zanyi, tunda so kike ki mayar dashi kamar wani jariri." Murmushi Amna tayi tace "Jariri ne mana, har yanzu baya iya kula da kanshi, Hamna yana buk'atar kulawa." Tsaki Hamna tayi tace "Ki kular min da yarana ni, banda lokacin haukanki ke da mijin na ki." Kashe wayar tayi ta aje ta sauko k'asa, madafa ta shiga su Zeituna na aiki ta kalleta tace "Aunty Zeituna idan kun kammala Amna tace a fitarwa mijinta da abincin saina kai mishi." Cike da sakin fuska Zeituna tace "Kin ganshi nan zan fidda mishi kuwa, dan bana mantawa da babban d'an gidan nan, tunda yau babu mai girka masa." Kallonta tayi tace "Amma kun gama da wuri yau aunty." "Eh saboda za'a kaiwa yan asibiti ne." Saida ta d'auki wanda Zeituna ta nuna mata tace "Wa zai kai musu?" "Ni nake son tafiya tare da Abban Fatima." Cewar Zeituna, kallonta Hamna tayi da mamakin sunan data kirashi dashi, wato tunda ita ma yanzu ta haihu dashi ba buk'atar ta ci gaba da kiranshi da Abban Ammar? Abun ya birgeta sosai har taji ina ma tana da 'yancin kiran d'anta da sunan ubansa data kirashi da *Shureim Ammar* da babbar murya kowa yaji, karb'ar abincin tayi ta fito ta nufi b'angaren nasu, ta manta bata saka ko da mayafi ba bare hijab, wannan siket d'in na atamfa da rigarsa wanda suka kama jikinta suka zauna daram dam, ga k'ibar data k'ara yasa k'ugun ta ya sake sama ya zauna da kyau, d'aurin kallabin mai sauk'i ne wanda zamu iya kiransa da ture kaga tsiya, dan ya turo sosai gaban goshinta, ko kwalli babu a idonta haka ta bud'a k'ofar d'akin ba tare da tunanin zata same shi a bud'e ba, amma sai ji tayi ya bud'e a hankali ta shiga tana kallon yanayin d'akin shiru kuma babu wuta sai hasken safiya kawai, saida ta je gaban teburin nan ta aje kwanukan ta nufi hanyar madafa dan d'ora ruwan d'umin kawai tayi tafiyarta, ta taka d'aya biyu na uku taji wata tattausar murya a bayanta yace "Ba sallama, ba neman izinin shigowa bare ki gaishe da mutane?" Tsayawa tayi sai jikinta da taji ya fara rawa rawa kamar zata kifa k'asa, had'e fuska tayi alamar bata son wargi sannu sannu ta juyo, inda taji maganar ta kalla sai taga ashe ya kishingid'a ne kan kujera yayi luf, turo baki tayi cikin shagwab'a tayi k'asa da kanta tace "Ina kwana." Wani narkakken kallo ne yake mata inda yake jin abubuwa da dama na b'abb'akowa daga k'asa suna yin sama, ganinta a haka ba k'aramin gigita nutsuwarsa tayi ba, a hakan daya ganta ta tuna masa da duniyarsa, dan atamfar ma kala d'aya ce haka d'inkin, kuma ita ma haka suka amsheta a ranar daya fara ganinta dasu, lumshe ido yayi tare da buk'atuwar son ganin hak'oranta ko da ba ta sigar dariya bane, hakan zaisa ya yarda cewa ta daina hushi dashi, amma ganin fuskarta a had'e a haka zai rikita lissafinsa har ya kasa iya aiwatar da komai, bud'a idon yayi ya sauke kanta yace "Kunna fitilar." Rintse ido tayi, har ga Allah tasan inta juya saiya kalleta, fuskantarshi tayi sai kawai ta dinga yin baya baya tana nufa wajen kunna hasken, murmushi ya dinga yi yana kallon fuskarta a ranshi yana godiya ga Allah data rufa masa asiri ta juya bayan, dan shi fa ko matarsa idan zata juya masa bayan nan sau dubu sai yaji buk'atarta sau dubun, kuma yana tsoron sake faruwar al'amarin a bisa wasu dalil...Hasken d'akin daya kawo ne ya katse masa tunaninsa ta hanyar kallonta. Da kallo ya bita ta shige madafa, wayarsa ya fito yana dannawa yana jiran fitowarta ya sata dariya ko hankalinsa ya kwanta. Ta d'an jima kafin ta fito rik'e da robar jiya da k'aramin towel, har gabansa ta aje masa ruwan kafin tace "Wai inji ta ka ci abinci ka gasa k'afarka sannan kasha magani." Murmushin gefen labb'a ya mata yace "Ashe kema kina jin maganar zuciyarki akai na?" Da sauri ta d'ago kai ta kalleshi da sauri kuma tayi k'asa da kanta saboda kallon da yake mata, ganin tayi k'asa da kanta yasa yace "Mai ladabin kunama, yanzu sai kin tashi zaki fita ki juyo ki ce min Allah ya isa ko?" A hankali ta girgiza kai tace "A'a, me ka min da zan maka Allah ya isa?" "Kinfi kowa sani." Yana kallonta, mik'ewa tayi zata fita yace "Baki k'arasa ladanki ba ai, ki zuba min abincin idan kin gama ki gasa min k'afar tawa, ko ba abinda tace kiyi ba kenan." Yamutsa fuska tayi tace "Ni ce zan gasa maka k'afar? To ba haka tace nayi ba, wannan ma saida ta rok'e ni nayi." Sakar masa duka giman idonshi yayi wanda hakan ya tsorata ta, ba shiri ta matso tace "Zan zuba to." Durk'usawa tayi ta fara zuba abincin, yana kallonta cikin taushin murya da alamar gaskiya ya karkace kai yace "Kiyi hak'uri Hamna, ki yafe min kinji." D'agowa tayi ta kalleshi babu alamar annuri a fuskarta tace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _53_ "Akan me zan yafe maka?" Cikin ladabi yace "Akan komai ma dana miki wanda ya tsaya miki a rai kike kallona da shi." Wata dariyar ka raina min hankali tayi tace "Abubuwan fa dayawa, ba zan iya ba gaskiya." Cikin wata siga yace "Yanzu kankana ba zaki iya yafe wa d'an uwanki ba? So kike mu tsaya gaban Allah ya mana hisabi? Ashe dama ba sona kike ba da kike so Allah ya k'ona ni, shikenan nagode." Rumgume hannayenshi yayi ya turo baki gaba alamar yayi hushi, kallonshi tayi ido cikin ido tace "Bana so gaskiya." "To ki yafe min." Ya fad'a da k'arfi yana gyara zama, girgiza kai tayi alamar a'a, dan haka ya d'ora gwiwar hannunshi kan cinyoyinshi yace "Saboda me?" K'asa tayi da idonta tace "Saboda suna dayawa." Cikin kafeta da ido yace "Fad'a min guda goma naji wanda suka tsaya miki a rai, ni kuma na miki alk'awarin duk'awa har k'asa na nemi affuwarki." Saida ta aje masa abincin gabanshi ta tsiyaya ruwa ta aje mishi sannan ta kalleshi tace _"Ranar da mukayi fad'a da Amna ka hukunta mu ta hanyar samu tsayuwar awa uku ba tare da mun motsa ba, a gaskiya ranar naji haushinka, saboda babu irin hak'uri da magiyar da bamuyi maka ba amma baka k'yale mu ba, sannan bana manta ranar daka sameni da saurayi na k'ofar gida kawai ka dinga zagina shima ka kore shi kace wai an min miji kuma mahaukaciya ce ni ya daina kula ni, har saida nayi kuka ranar fa."_ Cikin jin haushin ta ambaci saurayinta, wai saurayinta ko kunyarshi bata ji yace "Yanzu ma ashar d'in zan daddana miki idan kika kuma kallona kika fad'a min wai saurayinki." Kallonshi tayi tana k'yabta ido yace "To naji ci gaba." Cikin turo baki gaba tace "Shikenan ma kawai na yafe k'ananan laifukan amma ban yafe manyan laifukan ba." Mamaki ne yasa shi bud'e baki yace "Wanene kika yafe to wanene baki yafe ba?" Saida ta mik'e tsaye tana d'an jan siket d'inta sama alamar dakawa zatayi da gudu sannan tace "Kamar mari wanda ka min ba adadi, duka idan munyi laifi da zagi, sanda ka kusa sa min k'adangare a jiki, d'ora ni saman bishiya duk na yafe, amma ban yafe manyan ba har da keta min haddi na da kayi." Juyawa tayi da k'arfi zata zuba a guje yace "Dawo nan, in kika fita Allah saina biki." Tsayawa tayi ta juyo tana kallonshi kamar zatayi kuka, kujarar dake gefe ya nuna mata yace "Zauna nan." A hankali ta lallab'a ta zauna tana satar kallonshi, saida ya fara cin abincin kamar ba zai kulata ba kafin ya kalleta yana tauna lomar bakinshi yana fad'in "Wai ke kika haifi barewa ne ko kuma ita ta haifeki da ba kya gajiya da gudu?" Girgiza kai tayi ba tace komai ba, d'orawa yayi da "Zaki je asibiti ki taho tare dasu." Wani irin kallo ta masa, ta d'auka fa zai sake jadadda neman afuwarshi ne, amma ya canza maganar zuwa wata daban, mik'ewa tayi saida ta kai k'ofa ta juyo, rik'e da cokali ta ganshi zaisa bakinshi amma bai kaita bakin ba yana kallonta yana jiran ta juyo ta fad'i abinda zata fad'a, ai kuwa saida ta shirya gudu sannan tace "Ai ba sai ka fad'a min zanje ba, yer uwata ce ita baka fini sanin abinda ya dace na mata ba." Sakar mata ido kawai yayi yana kallo har ta fita a b'angaren, murmushi yayi mai sauti yace "Duka manyan ma zaki yafe Hamna da zaran kinji matsa." Tare da ita suka tafi asibiti kuma suka dawo tare, tana rik'e da macen jaririyar (ni dai bansan sunan da zan kira yaran nan na Ammar ba dan ya birkita min lissafi) suka shiga ciki, aje yarinyar tayi ta d'auko katifa ta mata shinfid'a a falo, inda Soueiba kuma ta d'ora mata ruwan wanka sai Zeituna data shiga kawo mata abinci mai lafiya da gina jiki, bayan ruwan sun tafasa ta shiga wanka su ma yaran aka fara musu ana canza musu kaya, ya shigo gidan da k'atuwar leda da kayan bebys ciki, Amna dake shan tsumagiyar kaba a hannun Husseina tana mata wanka ce ta dasa wata k'ara tana fad'in "Zafi, zafi Hajia ba zan iya ba, bana so wallahi ya isa haka." Kallon Zeituna yayi dake shafawa yarinyar kwalli yace "Uwa me take ma kuka ita kam?" Dariya tayi tace "Wanka ne ake mata." Zaro ido yayi yace "Da tafasashen ruwa halan?" Kai ta d'aga masa hakan yasa shi zabura ya nufi ban d'akin dake cikin falon yana fad'in "Na rantse da Allah babu mai toya min mata kamar yar wuta, ta gama azabar nak'uda kuma ta koma shan ruwan zafi, anya kuna da imani kuwa?" Soueiba ce tace "Ammar mu ne marasa imanin da muke taimakawa matarka? Kasan dai inba wankan nan aka mata ba da kanka wata rana zaka ce a mata shi." Juyowa yayi yace "Haba tanti, ni d'in banza da zan kiraku da marasa imani." Ban d'akin ya shiga saida Husseina taji tsoro, ita kanta Amna kunya ce taji ta kamata, kallon Husseina yayi da tace masa "Lafiya Ammar? Wani abu kake so?" Cikin taushin murya yace "Hajia bari na k'arasa mata wankan nan, naji sai ihu take mana daga wankan da bai taka kara ya karya ba." Tsaye ta mik'e rik'e da kabar hannunta ta kalleshi sai ta rasa me zata ce mishi ma, Amna na jin haka tace "Hajia ci gaba dan Allah, yah Ammar ka fita zan tsaya yanzu." Ummy na shigowa aka ce mata ya shiga kawai tabi bayanshi, tana zuwa ta tsaya bayanshi tace "Bawan Allah ko zaka iya basu wuri suyi abinda ya dace?" Juyowa yayi yace "Me zai hana kuwa Ummy." Kallon Husseina yayi yace "Ayi wanka lafiya." Juyawa yayi kamar zai fita saiya sunkuya cikin kunnen Amna yace "Karki bari ta k'ara k'ona min ke wallahi, inba haka ba ita ma saina mata wankan jegon nan, haka kawai ba za'a barki ki huta ba." Mik'ewa yayi ya fita Husseina ta bishi da kallo baki bud'e, kallon Amna tayi da mamaki tace "Anya kuwa Amna mijin nan naki zai bari a miki abinda ya kamace ki?" Ita dai k'ala ba tace mata ba kawai tana jiran taji saukar ruwan zafin, ko da ta gama shiryawa ma tuni gidan ya fara gaurayewa da yan barka. *Da dare* Jumare ta zo tare da Jumma suka ga yara suma, suna fita lokacin Hamna ta raka k'awarta Amie data zo ita ma, kusan a tare suka fita sai Ammar daya zo zai shigo, yana ganin Amie yace "Lah budurwata ce? Kina lafiya?" Kallonshi tayi ita dai har ga Allah matashin ingarman saurayin na birgeta, ko yanzu idan zai fito da niyyar aurenta saita aure shi, amma matsalar d'aya ta fahimci mutum ne da kanshi ke rawa, murmushi ta masa tace "Angon jego kasha k'arni, barka to Allah ya raya." Murmushi ya mata yana sunkuyar da kai yace "Har kin sani jin kunya wallahi, to ameen dai tunda addu'a kika min." Murmushi tayi ita ma ta mik'a masa hannunta tace "Ina tayaka murna sosai." Hannunshi ya mik'a mata shima suka gaisa yana fad'in "Nagode sosai, yanzu ya labarin soyayyarmu?" Sosai tayi murmushi tace "Labarin soyayyarmu kai zan tambaya." Saida ya kalli Hamna wacce ko da taga hannunshi da nata sun had'u taji bak'in ciki da wani mak'ok'on abu ya taso mata ta fara hararensu, Jumma da Jumare dake gefensu ne Jumare tace "Inna ashe d'an iska ne, kiga fa gaisawa yake da ita." Cikin sassauta murya Jumma tace "Rufa mana asiri Jumare karki sa ya jefa mu kurkuku." Kafin ya bawa Amie amsa ya kula dasu Jumare suna kallonsu, Jumma ce tayi saurin cewa "Ina wuni yallab'ai, dama Zeituna ce ta fad'a mana an samu k'aruwa shine muka zo barka, Allah ya rayasu akan sunna, saida safe." Daga yanda take magana ya nuna masa har yanzu a tsorace take dashi, cikin sakin fuska da fara'a ya amsa mata da "Lafiya lau, mun ko gode Allah ya saka da alkairi, ina baban namu?" Jumma ce tace "Malam yana gida yace dai a gaisheku." "Muna amsawa." Saida suka fara tafiya yace "Budurwata ya kike?" Tsayawa Jumare tayi wanda hakan yasa Hamna da Amie kallonta da kyau, tab'e baki Hamna tayi taja hannun Amie tace "Muke kinji, wannan duk yan matan garin nan ina ga fa nashi ne." Ita dai wuk'il ta masa da ido kawai sai shi daya matsa kusanta yana mata shak'iyanci wai saita fad'a asa tana son sa, Jumma ma dai matsawa tayi nesa dasu ta basu waje, saida Amie ta samu adaidaita sannan Hamna ta dawo, nan ta same su tsaye saida ta harareshi sannan ta nufi cikin gidan, yana ganin haka yace "Ke zo nan." Abinda ta tsana a duniya yace mata ke, kuma a gaban yarinyar nan yar k'auye zai ce mata ke zo nan, da k'arfi ta juyo cikin b'acin rai ta tsaya gabanshi tace "Gani lafiya?" Murmushi ya mata dan yana son cikata yace "Daga ina kike?" Saida ta sake had'e fuska tace "Daga inda ka aikini mana." Kallon Jumare yayi yace "Kinji gani ko? Da ita ce zan aura to matsalar k'walwa gareta, shiyasa nake so na aureki Jumyta dan naga uwata Zeituna tana da hankali nasan ke ma kamar ita ce." Bud'a baki tayi zatayi magana sai kuma ta kasa ta kalleshi da tsananin mamaki ta kalli Jumare data kalleta, sake d'aga labb'enta tayi sai taji sun mata nauyi, amma fa ya wulak'antata mutumin nan, kallon Jumare tayi rai a b'ace cikin d'aga murya tace "Ke bar nan wajen kafin na miki dukan tsiya." Baki Jumare ta saki kawai saita yarda da abinda ya fad'a, ganin ko niyyar barin wurin ba tayi ba yasa ta sake d'aga murya tace "Zaki b'ace ne ko saina karyaki a wurin nan." Da sauri Jumare ta wuce sai kuma ya bita da dariya, yana cikin k'yalk'yala dariya ya kalleta sai kuma yayi tsitt kamar ba shi ba, saida ta harareshi sama da k'asa tace "Idan ni mahaukaciya ce kai kuma fa? Mai kula dani?" Tsaki tayi ta shige cikin gidan inda ya sake bushewa da dariya yana cije leb'en kasa shima ya shiga, kai tsaye b'angarensu ya nufa, tun a k'ofa yake jin kukan Amna k'arama, yana shiga ya ganta hannun Amna sai nono take saka mata tak'i karb'a sai harshenta ke rawa tsabar kukan da take cancarawa, kakanni kam sai sharri ake mata suna kiranta da mai la'ana kamar uwarta, tak'im tak'im yaje gabanta yasa hannu ya amsheta ya fara jijjigata ya nufi d'aki da ita, bayanshi Amna tabi dan tana so ta fad'a mishi abinda take so, yana jin motsinta a bayanshi ya juyo yace "Wai me aka mata ne take wannan kukan?" Kafin ta bashi amsa yaja hannunta ya zaunar da ita bakin gado ya d'ora mata ita a k'afa yace "Bata tasha." A hankali ta fito da nonon dake mak'ale a k'irji ta d'aga kan jaririyar sosai tana so ta sa mata, amma daya shiga bakinta sai tak'i kamawa, cikin d'aga murya yace "Wai lafiyarta k'alau kuwa? Naga lafiya lau take yau." Kallonshi tayi tace "Yah Ammar kawai fa dan an mata hujen kunne ne take wannan kukan?" "Me?" Ya fad'a da k'arfi yana k'are mata kallo, cikin yanayin da yake nuna zai iya tabka rashin mutumci yace " Amna wannan yarinyar ce kika sa aka ma hujen kunne? Kuma shine har kike cewa wai dan an mata, wai ma ne kenan?" Nufa yayi wajen coiffeuse (dressing miror) yana fad'in "Yau na tabbatar da ke baki da hankali har da ma wacce ta mata hujen, amma zan nuna muku ni na dameku na shanye wallahi, inba raina mutane ba yarinyar da aka haifa jiya, ke kikayi nak'udarta amma a gaban idonki ana juheta kina kallo, to ko de bake kila haifeta bane?" Ya juyo yana kallonta, ita dai kallonshi take tana so kuma ta kama nonon, tana kallonshi ya fito da yan kunnanta na ziraniya da Hajia ta siya mata da kud'in daya bayar ya nufo kanta, ita dai bata san me zaiyi ba ta kuma kasa tuna girman abinda zai aikata, karb'ar yarinyar yayi ya aje gefe duk kukan da take kuwa, idonta ya kalla ya rik'e k'ugu yace "Ke mahaukaciyar ina ce Amna?" Cikin fara tsorata da yanayinshi ta fara matso k'walla ta girgiza masa kai, nuna k'aramar Amna yayi yace "To uban wa yace ki yarda a mata huje tun yanzu? Waje zaki fara aikata ne tun yanzu da kike son ganin ta fita da kyau? Ko kuma idan ba'a mata yau ba shikenan zata mutu ne? Me zaisa ba za'a bari har ta k'ara wayo ba? Kawai tsabar rashin imani irin na ku Amna ku kama min 'ya ku huje mata kunnuwa, kuma ni abun bak'in cikin ma shine a gabanki, kuma wai har kike cewa wai dan an mata huje, kiji fa wai dan an mata." Saida ya saita d'an kunnan hannunshi ya fizge hijabinta yana k'ok'arin rik'o kunnenta yana kallon yarinyar da har yanzu ke kuka yana fad'in "Ke yi shiru abinki yarinyata, da ubanki fa a raye waye zai takaki a garin nan? Ai ban ganshi ba na rantse da Allah, bari kiga yanda zan d'au maki fansar cin kacar da aka miki, yo mu rashin mutumci ai gidanshi ne aka zo har na siyarwa muna da." Amna na ganin yana shirin burma mata kunne huje na uku kenan dan dama biyu garesu ita da Hamna, zabura tayi zata bar wurin ya kwantar da ita kuma tsaf yayi zaune kan ruwan cikinta, had'e hannayenta tayi wuri d'aya cikin fad'uwar gaba da kuka tace "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri, Allah wallahi ba zan sake ba na rantse maka." Juya fuskarta yayi ko saurarenta baiyi ba ya saita daidai huje na biyu wanda ke sama ya turtsa mata d'an kunnen nan, wata uwar ihu ta saki jin abun ya zo mata bata shirya ba, cikin azaba da rad'ad'i ta fara fad'in "Dan Allah kayi hak'uri ba zamu k'ara ba yah Ammar, zan mutu wallahi dan Allah ka d'aga ni na tuba wallahi." K'ok'arin juyo d'aya b'angaren ya shiga yi yana fad'in "Yo ku k'ara mana, ai ba musaki bane ni da zan kasa rama mata ba." Da k'arfi ya juyo d'aya b'angaren ya janye hijabinta nan ma ya jawo kunnen ya saita shi, shima burmuk'a mata yayi na uku kafin ya d'agata yana d'aukar yarinyar yace "Shiru shiru yar baba, tuni ubanki ya d'auki fansa, a shirye muke da duk abinda zai faru ya faru, ba tsoron bala'i muke ba." Ummy da taji kukan yarinyar ya k'i k'arewa kuma k'arshe taji na uwar yasa ta shigowa d'akin ko sallama ba tayi ba dan tasan d'anta ne ke wani mugun abun, ai kuwa ta samu Amna sai sharar hawaye take da hijabi tana rufe kunnenta, matsowa tayi tana musu kallon tuhuma tace "Me ka mata ita kuma?" Kallonta yayi yace "Ki tambaye ta Ummy tasan abinda tayi." Kallon Amna tayi tace "Me kika mishi?" Cikin rage sautin kukan tace "Ba komai Ummy, marata ce ke ciwo." Kallon tuhuma ta masa dan bata yarda ba, jinjina kai tayi tace "Karb'i yarinyar ki zo falo to." Mik'ewa tayi ta tara masa, saida ya kalli idon Amna yace "Gata nan amana na baki, aka sake cutar min 'ya sai ranki ya b'ace." Juyowa Ummy tayi ta kalleshi jin abinda ya fad'a, shima kallon Ummy yayi yace "Ummy waya ma yarinyar huje saboda Allah?" Da d'an mamaki tace "Tantinku ce *Zuweira*, da matsala ne?" Jinjina kai yayi ya nufi kan gadon ya d'auki yan kunnen daya ma Amna huje dashi yace "Yau ko zata ga rashin mutumci wallahi, dama ba shiri muke da ita ba saboda tana kirana da mai kamar shaye shaye, to yau zan mata aikin da ko mai shan cocaïne ba zai mata ba." Da sauri Amna ta rik'e rigarshi ta baya ta kalleshi tace "Dan Allah yah Ammar ka rufa masa asiri, kasan halin tanti Zuweira fa." "To sai me? Ita tasan nawa halin amma kuma ta aikata min wannan ta'asar." Ummy dake kallonsu cikin rashin sani ne tace " Wai miye ya faru?" Da sauri Amna ta kalleta tace "Ummy dan Allah ki bashi hak'uri karya je." Kallonshi Ummy tayi tace "Miye wai?" Ba tare da fargaba ba yace "Ummy huje aka mata bata isa ba, shine zan rama mata." Zaro ido tayi ta matso kusan Amna ta d'aga hijabinta, tana ganin kunnenta ta kalleshi rai a b'ace tace "Me kayi haka Ammar? Me yasa wai kai duk abinda ya sab'a ma hankali shi kake aikatawa? Hujen daya zama dole dan an ma yarinya shine ka rama kan uwarta, me kenan hakan ke nufi? Ka fita k'aunarta ne?" Cike da rashin ko in kula yace "Haka aikinta ya nuna bata k'aunarta." Cikin jin haushi ta nuna mishi k'ofa tace "Fita a gidan nan, ko ko k'ala ban yarda ka fad'a ma Zuweira ba in dai ni na haifeka." Saida ya rusuna yace "Angama." Fita yayi yana zuwa falo yayi tsaye yana kallon Zuweira dake shan kunu a babban roba tana ta hira abinta, saida ya rik'e k'ugu ya dinga motsa bakinshi yana fad'in "Shirgegiyar wofi, ki samu yar jaririya ki taushe da uwar cinyarki ki mata hujen, kuma tana kuka hankalinki kwance kina shan kunun da ubanta ne ya siyo hatsin yake biyan ruwan da aka dama kunun, kai amma matar nan fa akwai yar rainin hankali, yau kinci albarkacin Ummy da sai na cire miki zaninki ta kai, amma ba komai ai akwai wata rana." K'wafar da yayi ce tasa hankalin wasu dawowa kanshi wanda basu kula dashi ba, Ummy suna fitowa tana fad'a ma Amna cewa "Kiyi hak'uri kinji, kar ma ki bari kowa ya sani, ki k'yale shi kawai." *A gurguje fan's* Komai ya tafi daidai inda Ammar yayi iya bakin k'ok'arinsa wajen gwangwaje amaryar jego da yaranta, saida ya mata d'inki kalar shida na tanfatsa tanfatsa leshi da shadda, ranar suna kuma kamar yanda ya fad'a ne sunansu ya mayarwa yaranshi, ranar biki gidanshi dake nesa da nan suka zauna shi da abokansa inda Amar dasu Junaid suka d'auki nauyin abinci da abin sha. A gida kuma ko Hamna saida sukayi d'inki har kala uku ita da Amna, anci an sha anyi bidiri sosai an gode Allah sai fatan Allah ya raya yaran. Bayan kwana shida kuma akayi bikin Jamila ita ma, bayan biki Zeinabu ta so ta koma d'akinta sai Jibril yace kawai su barta har ta gama wankasaita koma. Umaimah ce kawai yanzu ake jiran haihuwarta, cikin ikon Allah kuma saida ta shiga wata na goma sannan ta haifi 'yarta ita ma masha Allah, haka akayi shagalin sunanta aka gama lafiya. Kwana biyu da kammalawa Hamna ta rok'i Hajia ta barta ta tafi Abuja wajen koyon kwalliyarta, ta tafi kuma tana yin abinda ya kaita cikin kwanciyar hankali, sati biyu ta d'auka kafin ta dawo gari, Gambo dake hushi da ita na tafiyarta basu sani ba ne ya sauka yanzu da sa bakin Hajia ya bud'e mata gwangwajejiyar salon da babu abinda babu, sabuwar duniya kuma sabuwar rayuwa gareta, tana zuwa aikinta kuma tana yinshi da himmada kulawa saboda tana so, tana iya zuwa ko ina saboda yi wa wasu kwalliya kamar amarya ko mai jego. *Shekara d'aya* A cikin shekara d'aya abubuwa dayawa na ta faruwa, wasu na farin ciki wasu na bak'in ciki wasu na jimami, Hamna kuma yanzu mota take hawa tana murzata duk inda take so, sai dai har yanzu taka tsantsan take wajen nunawa yaronta soyayya, wanda yanzu ya saba da ita sosai yana kiranta da *Tata*, lokuta da dama idan ta ga Ammar da yer uwarta suna rayuwar farin ciki sai taji kowa a gidan yana bata haushi, takan ji kamar an daketa kuma an hanata kuka ne, amma aikinta yana d'an d'aukar hankalinta zuwa wani wurin. Yau ma kamar kullum ko da Amar ya shigo ya samu Umaimah a yanayin daya fi samunta kullum, tsaki kawai yayi ya shige d'akinshi bai kulata ba, saida gabanshi ya fad'i ganin Farisa k'anwar Jibril ta zage tana gyara shinfid'ar gadonshi, cikin mamaki yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _54_ "Farisa me kike yi a d'aki na?" Ba tare data d'ago ba ta juyo dan ganinshi, hakan ne yasa rigarta dake da sakakken wuya k'irjinta ya fito har yakan iya hango matashiyar inda nononta suka taso, lumshe idonshi yayi ya d'an kawar da kanshi yana sauraren muryarta da yaji yau ta masa daban tana fad'in "Sannu da zuwa yah Amar, aunty Umaimah ce tace na gyara maka d'akinka." Bud'a idonshi yayi ya sauke su kanta, wani tartsatsi yaji tare da mummunan fad'uwar gaban da baisan da zuwanshi ba ya ziyarce shi, daga k'asa har sama ya kalleta kamar yau ne ya fara ganinta, yarinyar duka shekara ta sha biyar ce take ciki yanzu, amma da yake tana da girman k'asusuwa saika d'auka ta wuce shekarun, a yau dai kuma a yanzu take sai yanzu kibiyar sonta ta harbeshi babu shiri, da fari yayi niyyar mata kashedin karta sake shigo mishi d'aki ne, amma ganinta a cikin riga da siket na katin da suka karb'eta sun tafi da masifar da damuwar duk daya shigo dasu, saida ya gyara murya ya saitata ya lumshe ido yace "Ok, ci gaba." Jiki a sanyaye ya juyo ya fito, yanda ya barta ya sameta tana ba wa *Khairat* nono, kusa da ita ya matsa ya tsaya gabanta yana ma yarinyar magana, tana jin muryar babanta tayi tsal ta diro daga kan cinyarta ta mak'ale mishi, d'aukarta yayi duk da bata cikin yanayi mai kyau yarinyar, dan kayan jikinta ma basu da kyan gani sai k'arnin nono take, zaune yayi kujera mai fuskantarta ya d'ora Khairat kan cinya ya kalleta da kyau yace "Umaimah, domin Allah in zaki fad'i gaskiya kina ganin haka ya dace kuwa ki tura yarinya har d'akin bacci na wai ta gyara min? Ke kuma gaki zaune ba kya komai." Cikin fad'a fad'a tace "Bana komai fa kace? Yanzu baka same ni ina bawa yarka nono ba, ko shi ba aiki bane? Yanzu haka girki na kan wuta ban sauke ba, kuma kafi kowa sanin ina da aikin yi tunda ba zaune nake gida ba, dan lokacin da zan dawo gidan haka kawai saina kashe kaina wajen bautar gyaran gida." Wani kallo ya mata yace "Kashe kaine ke a ganinki?" Kawar da kai tayi tana jan tsaki hakan yasa ya girgiza kai yace "To kiji da kyau, indai har ke baki da lokacin gyara min d'aki na karki k'ara baiwa kowace yarinya damar shiga d'aki na dan ta min gyara, inhar kinsan ba zaki iya ba ki ban makullin d'akina dana baki saina dinga gyarawa da kaina, kinji na fad'a miki." Yana fad'a ya mik'e da Khairat suka fita daga d'akin, mik'ewa tayi ita ma zuwa madafa tana fad'in "Masifaffe kawai, sai kace wani tsohon daya gaji da duniya, ka k'i tamnuwa ka k'i had'uwa kullum da b'acin ranka nake kwana, duk abinda nayi banyi daidai ba." Yana shigowa da sallama yaran biyu suka tafi a guje suka rumgume shi, kan Huda ya dafa yace "Beby ya kike?" D'aukar *Abdul maleek* yayi ya kamo hannunta suka zauna, Jamila data zubo ma Huda abinci ce cikin jin haushin yarinyar ta aje mata kwanon k'asa tace "Ke." Juyowa Huda tayi ta kalleta, shi ma idon ya sakar mata inda ta nuna mata abincin tace "Wuce ki zauna ki ci abinci ki je ki kwanta, na gaji da hayaniyar nan ba zan d'auka ba." Cikin sanyin jiki ta nufi inda ta nuna mata ta zauna, girgiza kai kawai yayi ya mik'e ya aje Abdul ya shiga d'akin shi, bin bayanshi tayi ta fara taimaka masa wajen cire kaya ya dakatar da ita ta hanyar fad'in "Jamila me yasa ba kya sakin fuska ga yarinyar nan? Ita ma kamar 'yarki ce." Kallon idonshi tayi tace "Ba dai 'yata ba yarka ce, da ta hanyar aure aka sameta zan iya mata wannan gatan." Girgiza kai yayi ya nufi ban d'aki hakan ya b'ata mata rai tace "Wai meye haka? Shikenan kullum mun dinga samun matsala da kai akan waccen yarinyar, akan me zata shiga rayuwarmu tana neman hana ni jin dad'in rayuwa, duk abinda nake mata baka gani?" A hassale ya juyo yace "Me kike matan? Kina mata sutura ne ko kuma ke kike mata wanka, ke kike nemo abincin da take ci? Dafawa ne kawai naki, kina biyan kud'in makarantar ta ne ko kuma ke kike kaita? Ko kaya wannan kina saka mata? Yarinyar nan a gidan nan take rayuwa, amma ba'a b'angaren nan ba, saina nemi alfarma wajen Mama kad'ai take bani ita ta zo nan ta kwana, baki tab'a wahala da ita ba na d'ai rana, amma har ki bud'a baki ki ce min wai duk abinda kike mata, to wace tsiyar kike mata bayan nuna mata k'iyayya kuma a gabana." Juyawa yayi zai shiga tace "Yanzu a kanta ne kake d'aga min murya haka?" Sake juyowa yayi yace "An d'aga miki kiyi abinda zakiyi?" Saida ta matso kusanshi tace "Kasan ina da abunyi da dama, amma ina so ya zama na k'arshe ne wannan, dan haka in ka gaji da zama dani ka ban takardata na tafi gidanmu, ni kaina na gaji da wannan auren." Saida ya mata murmushi yace "Kije, da safe zan aiko miki da ita, yanzu banda lokacin rubutu." Hararanta yayi sama da k'asa ya shige ciki, jingina yayi a jikin bango yana sauke numfashi, yana son zama da Jamila sosai fiye da yanda take tunani, amma bai tab'a tsammanin raini irin haka zai shiga tsakaninshi da ita ba, sam yanzu bata ganin girmanshi, kuma yana b'oyewa ne dan baya so iyayensu su sani, amma ta fara kaishi bango. Jin ta buga k'ofar d'akin da k'arfi yasa shi fitowa shi ma da sauri ya bi bayanta, ko kallon Abdul ba tayi ba da Huda ke bashi abinci ta fita da mayafinta, da gudu gudu ya bita yana kiran "Jamila saurare ni, Jamila, dake fa nake magana." Tana bud'a k'ofar b'angaren nasu daidai Ammar ya fito daga nasu b'angaren, tsayawa tayi da niyyar ya wuce saita shige ita ma, amma saiya tsaya yana musu kallon tuhuma, Jibril ya kalla yace "Lafiya kake gudu kai kuma? Ina zaki je?" Ya jefa mata tambayar yana kallonta, sunkuyar da kai tayi gabanta na d'an fad'uwa, Jibril kam yana ganin Ammar yaji sanyi dan yasan babu inda zata je, ai bai tsaya b'ata lokaci ba yace "Yah Ammar wai ita nan fa yaji ne zata yi." K'ank'ance ido yayi ta kalleshi ya kalleta yafi sau ashirin kallon daya musu, saida ya jawo hannun Jibril ya zo kusa dashi sannan ya nuna ta yace "Yanzu kai domin Allah wannan yarinyar ce zatayi yaji kuma shine kake binta da gudu? To tayi yajin mana, barkono ma ya ci ubanshi." Tureshi yayi baya yana fad'in "Dallah matsani daga nan." Kallonta yayi cikin tsawa yace "Kalleni nan." Cikin turo baki ta d'aga kai ta kalleshi, saida ya kalli Junaid yace "Idan ta tafi ka je ka fad'a min, ni kuma har d'akin tanti Zeinabu zan same ki wallahi in cire miki hak'ori." Cikin d'aga murya sosai yace "Malama wuce min ciki ko." Da sauri ta juya ta shiga ciki tana fashewa da kuka, Jibril ya juya zai bita ya rik'oshi yace "Kai sakaran wane gari ne? Yarinyar data tashi gabanka zaka zauna tana maka iskanci, kai ala wadaran naka ya lalace." Sakinshi yayi ya juya da sauri ya sameta shi kuma ya wuce b'angaren Hajia, dama dai har yanzu ba sallama yake yi sai randa yaga dama, Shureim dake ta wutsilniyarshi tsakiyar falon yana ganinshi ya taho da gudu kamar zai fad'i, da sauri ya d'aukeshi yana juyi dashi, kallon fuskarshi yayi yace "Ina Ummy?" Juyawa yayi ya nuna masa k'ofar d'akinta alamar tana ciki, nufa yayi dashi suka shiga d'akin da sallama yanda ba kowa yaji ba, Ummy na zaune da wasu takardu tana dubawa ta bishi da kallo har ya tsaya gabanta, cikin tausar da murya yace "Ummy barka da dare." Saida ta mayar da dubanta kan takardun tace "Wani abu kake so ne?" Murmushi ya mata yace "Eh Ummy." D'agowa tayi ta kalleshi inda ya fara fad'in "Dama gobe zamu je wajen tanti Hadiza ne, shine nake neman alfarma ki bamu Shureim mu tafi dashi." Sake d'aga kanta tayi sosai ta kalleshi, ba zata hana shi ba, amma kuma bata san me yasa kullum yake k'ara kusanci da yaron ba, saida ta sake duk'ar da kanta sannan tace "Ba damuwa, amma ka kula min da yaro na, ba zan lamunci komai ya same shi." Murmushin gefen labb'a yayi yace "Dan na baki tabbaci akan kulawar da zan masa Ummy ba ma zan tab'a cewa shi d'in k'ane na ne ba, sai dai nace *d'ana* na fari ne." K'uri ta masa da ido, me yake nufi? Ita ma al'amarin Ammar d'in nan wani lokacin kamar mai shafar aljanu, k'ala ba tace mishi ba sai juyawa da yayi ya fita yana d'auke dashi, suna fitowa farfajiyar Hamna ta shigo tana gyara siririn mayafinta dake kan kafad'a da jakarta a hannu, tana ganin Shureim ta saki murmushi inda shima yaron ya fara d'aga mata hannu yana son yaje wurinta yana fad'in "Ta..ta." Da sauri ta k'araso tasa hannu d'aya ta tallabo bayan yaron da nufin ta karb'eshi, amma sai Ammar ya rik'eshi ya k'i sakar mata shi yana kallonta, a zuciyarshi yake fad'in "Oh Allah, yaushe al'amarin nan zai k'are ne?" Kallonshi tayi tace "Malam bani yaro na mana." Kallon daya mata yasa ta kawar da kai tana lalabar cikin jakarta, chocolate ta fiddo ta bawa Shureim tare da juya mishi kumatunta tace "Bizou." Sumbatarta yayi hakan yasa ta mishi dariya, Ammar ta kalla ta had'e fuska, zata wuce ta barsu yace "Ke daga ina kike?" Cikin matsanancin jin haushin yace mata ke ta kalleshi cikin d'aga murya tace "Ban sani ba, ban sani ba Ammar." Murmushi ya mata na jin dad'in ya cikata, ta juya ya sake cewa "Ke meye sunan turaren nan naki? Naji shi kamar na yan bori." Juyowa tayi cikin mayar da martani tace "Aljana barhaza ce iyakar borin." Ta juya zata shige ya rik'o hannunta, cak ta tsaya amma bata juyo ba, idonta ne suka cicciko da k'walla ga fad'uwa da gabanta yayi, tsikar jikinta duk ta tashi ga jijiyoyinta da taji duk sun saki, cikin tausasa murya yace "Gobe zamu tafi wajen tanti, ko zaki je ke ma?" Bata uya juyowa ba sai kai data girgiza masa alamar a'a, sakinta yayi zata shige yace "Tare da Shureim zamu tafi, Ummy ma ta amince." Juyowa tayi da sauri ta kalleshi sai hawayen suka taho mata, da sauri ta matso kusanshi kamar zata fad'a jikinshi sai kuma ta tsaya, marairaicewa tayi duk tayi kalar tausayi tana matsar ido cikin raunin muryar kuka tace "Ammar ka hutar dani dan Allah da zuciyata, na gaji wallahi Allah ba zan iya jura ba, ka daure ka dinga yin nesa dani kaji." Shi kanshi saida ya lumshe ido yanda ta k'arashe maganar, kallonta yayi da idon fahimta da kuma basira, idan ya fahimta daidai abinda ke d'awainiya dashi shi yake galabaitar da ita, to amma ya zasuyi? K'addararsu ce haka, yanda suke kallon juna ne yasa Hamna saurin kawar da kanta ta juya da gudu ta shiga ciki, saida Hajia ta bita da kallo ita dake zaune wurin, tana shiga d'aki ta fad'a kan gado ta fashe da kuka, sosai take ruzgar kuka kamar wacce aka wa mutuwa, ko wanka bata iya tashi ba saida taji wayarta na kuka, fito da iya tayi a jaka ta duba, wani Alhaji ne da yake matuk'ar sonta yake bibiyarta amma Allah yasa ta kasa bashi ajiyar zuciyarta, ba wai shi kad'ai ba akwai irinshi bila adadin da suke bibiyarta amma ta kasa bawa ko d'aya dama, aje wayar tayi ta ci gaba da rera kukanta da tunanin mafita a rayuwarta. *Da safe* tsaf suka shirya dan tafiya, kaya kala d'aya Ammar yasa tare da yaran har Shureim, Amna ma cikin wani had'add'en leshe ta shirya kalar kwalliyar aikin kayansu, suna gaishe da iyayen suka musu sallama suka fito, har zai bud'a motarshi yaji Amna na fad'in "Yer uwa dama baki fita ba? Ai na d'auka kin tafi shiyasa ban shiga d'akinki ba." Ko kallonta ba tayi ba tace "Amma ai da kin tambayeni da an fad'a miki ina nan ko bana nan. Juyowa yayi ya kalleta, kamar dai yanda yanzun tafi zama yanzu ma hakane, doguwar rigar bak'in leshe ce jikinta d'inkin simple amma ya hau jikinta sosai musamman wajen mazaunanta, d'aurin d'an kwalin ma kawai tayi shi ne simple, fuskarta ma tayi fes da ita babu komai data shafa mata, amma k'amshin tattausan turarenta kad'ai zai iya kwantar maka da hankali, wayarta gyalenta da makullin mota duk a hannunta suke, Shureim ne ya tafi wajenta ta d'aukeshi tana mishi magana, matsawa tayi kusanta tace "Yer uwa idan baki da aiki sosai me zai hana ki zo muje tare, Mama zatayi farin cikin ganinmu gaba d'aya a tare." Kallonsu tayi dukansu, Ammar k'arami ne ya zo kusanta shima yana d'aga hannu sai Amna dake mak'ale wajen Mamanta, murmushi tayi ta kalli Ammar tace "Sai dai muje a mota ta, bansan ko mijinki ya lak'a min bom d'in da zata tashi dani ba." Kallon daya mata tare da cije leb'enshi yana wani shegen murmushi yasa ta kallon Amna dake dariya tace "Taya kike tunanin zai tasar min yer uwa, kuma ko ba komai ai ni da yaranshi duk muna cikin motar." Motarta ta nufa tana mik'a masa makullin tace "Bismillah." Hararanta yayi yace "Drebanki ne ni da zan tuk'a ki?" Jefa mishi makullin tayi ta bud'a gidan baya ta d'auki yaran d'aya bayan d'aya duk ta zaunar dasu, har zata zauna ya jawo ribom d'inta daya fito waje ya shiga wajen yaran ya zauna yana fad'in "Ba inda zan tuk'aki kinji yarinya." Cikin jin haushi ta kalleta ta cire d'an kwalin ta mayar da ribom d'inta ta d'aura kallabin, zatayi magana Amna ta zagaya wajen mai tuk'i tana fad'in "Ya isa dan Allah, zauna nan ni saina tuk'a." Lek'owa yayi daga ciki yace "Ke duniyata fita a idona in rufe, ai da kinga kina tuk'i to ki tabbata tukunyar tuwo ce ko kuma kan gado kike kina wainani son ranki, amma ba dai mota ba." Sunkuyar da kai Amna tayi ta dawo gaba inda Hamna ta kalleshi tayi tsaki tace "Anji sanyi ba'a rufa ba Ammar, wai kai yaushe zaka girma ne?" Ko kallonta baiyi ba yace "Ranar dana samu isasshen nono nasha." Wani kallo ta masa mai nuni da cewa ashe ni ce banda hankali, saida ta shiga ta zauna tana mak'ala mad'aurinta tace "Yace baya so ki tuk'a mota mana saboda yana takaicin ya siya miki." Saida ya d'auki Ameera ya d'ora kan k'afarshi yace "To banda kud'i, yan gidan nan naku kuma kowa taurin zuciyar tsiya ne dashi, k'aramin abu baya sa zuciyarsu ta kusa tsayawa bare na samu kud'i ta hanyarsu, dubi kakar nan taku kwanan baya mun d'auka zata shek'a ne amma ta tashi da ranta kuma." Dariya suka bushe da ita Hamna har da rik'e ciki, tayar da motar sukayi taja suka fita, tun kafin ta hau titi yace "Ke kin tabbata dai kin iya tuk'i ko? Karki zo ki jawo min mutuwa, burina nan gaba duniyata ta haifa min yara goma sha d'aya." Kallon Amna tayi tace "Ki ce mijinki ya min shiru akwai abubuwa da nake so su zauna min a kai, dan in ya ci gaba da surutun nan na tabbata saina manta har sunana ma." "Haka kawai malama saina rufe baki na, babu wanda ya isa ehe." Tafiya suke sosai cikin farin ciki dan dariya kawai yake basu suna karb'a, duk yanda Hamna take son ta dake ta fita shirginshi abun ya gagara, idan yayi wata katob'arar dole take darawa, yanzun ma yara duk sunyi bacci, kallon Hamna yayi ta madubi yace "Kankana wai ina budurwata ne?" Saida ta nuna alamar b'acin rai tace "Wallahi Ammar karka sake kirana kankana, na fad'a maka bana so ko." Amna kuma tana juyowa tace "Wacece kuma budurwarka?" Kallonta Hamna tayi tace "Amie, ita yake so ita kuma bata da lokacin shi, ya addabeta nima kuma ya addabeni, na fad'a masa idan ya k'ara min maganar ta zan fad'a miki dan ba zai yiwu na ci amanarki ba." Dariya yayi ya kalli Amna yace "Ya kike kallona? Ki fad'a mata mijinki mai lafiya ne ire irenku goma ma zan iya ji daku." Juyowa Hamna tayi baki bud'e tace "Bala'i, ire irenmu ko ire iren matarka?" Saida ya kalli tsakiyar idonta yace "Ku nace, dukanku dake da ita da takwas kamar ku." Sun d'auki awa d'aya a k'alla kafin suka isa dan ba gudu take ba, kamar yanda suka yi tunani kam hakane ya faru, Hadiza da Chua'ibu sunyi farin ciki sosai na ganinsu tare, sunyi walwala sunyi hira da mahaifiyarsu sosai, inda daga k'arshe Hadiza ke tambayar Hamna ya labarin aure, kamar dai yanda ta saba yanzun ma cewa tayi kawai tayi ta mata addu'a, har yanzu bata samu wanda ya dace bane, amma data samu zasu ji labarin aurenta ita ma, Amna ce ta kalli mahaifiyarsu tace "Mama wallahi tana da samari masu nutsuwa da hankali, kawai bata shirya aure bane, amma kar kiga manyan mutanen dake zuwa wajenta gida." Cikin jin haushi tace "K'arya nayi kenan? Ina ruwanki da maganarmu? Karki koma saka min baki." Kallon mahaifiyarsu tayi zatayi magana Hadiza tace "Dakata Hamna, inhar kinsan gaskiya ne abinda ta fad'a to kiyi gaggawar tsayar da mijin aure, Hamna ba zan ji dad'i ba yau idan kika lalata mana sunan zuri'a, duk da ba a hannuna kuka tashi ba amma Hajia zata d'ora min laifin gurb'atarki, dan haka ina rok'onki dan Allah ki fitar da miji kiyi aurenki ki huta tun kafin girma ya k'ara kamaki, mace ce ke d'an lokacinki k'alilan ne, sannan idon mutane dayawa zai iya komawa kanki duba da aikinki da kuma abinda kike hawa yanzu, ki taimaka kinji ki rufa mana asiri da ma kanki." Saida tayi k'ok'arin had'e kukanta tace "Naji Mama." Hararan Amna tayi da take ganin ita ta had'ata da Maman, dariya ta mata ta mik'e ta fita daga d'akin, cikin nutsuwa Hadiza ta sake kallonta tace "Hamna, ki tabbatar min da wani abu d'aya mana." Kallonta tayi hakan yasa ta cewa "Ki kula da kanki, ki kare mutumcinki kema bar ki kaishi inda ya dace." Kasa tsayawa sukayi sai kawai suka zubo mata, cikin tausayin kanta ta fad'a k'afar maman tana kuka, hakan ne ya tayar mata da hankali ta fara tambayarta "Hamna lafiya? Daga magana, ko wani abun ne ya faru?" Girgiza kai kawai tayi amma ba tace komai ba, da k'yar ta rarrasheta sai ajiyar zuciya da take saukewa. *A da* malam Rabi'u kad'ai take shakka, amma yanzu har shi d'in ta daina tsoronshi musamman daya k'ara tsufa, fita ma bai cika yi ba inba masallaci ba ko wani abu daya zama dole, a baya mai zaman kanta ce, amma yanzu bayan rabuwar aurensu da Junaid ta zama karuwar gida, tana fita sanda take so ne kuma ta dawo sanda ta ga dama, kakarta ta rasu wata biyu da suka wuce daga ita sai mahaifiyarta yanzu a gidan, bud'ewar idonta yanzu babu inda bata zuwa neman kud'inta ta dawo, mahaifiyarta ta zubawa sarautar Allah ido, dan maganarta ba dama ba sosai take fitowa ba har yanzu bare kuma ta mata fad'a sosai har ta jita, sai dai fatan shiriya kawai ta gari. Sai bayan magriba suka shigo gari, gaba d'aya falon Hajia suka yada zango suna sauke gajiya, Amna da duk bata jin dad'i ne take k'ok'arin gyara zamanta amma Ameera ta hana ta damar haka, cikin saurin hawan da bata san ko na meye ba ta d'an tureta tana fad'in "Dan Allah Ameera ki matsa min na huta, haba ke kenan sai lak'uwa." Kallonta Ammar yayi ya kamo hannunta yana fad'in "Ke taho nan kinji, rabu da uwarki ta ji da d'an k'anninku wanda ke neman koya mata masifa." Kallon kallo dai kawai akayi amma babu wanda yace wani abu, sai Amna cikin tausa murya tace "Wane k'aninsu kuma?" Murmushi ya mata yace "Na cikinki mana da zai iya kai tsawon wata biyu zuwa d'aya da rabi." Shiru kawai tayi ita ma sai tunanin maganarsa data fara, suna haka Junaid ya shigo da sallama da kuma fara'a a fuskarshi, gaisawa sukayi kafin ya matsa kusan Hajia, yanda yake sunne kai yasa ta kalleshi tace "Ya dai malam?" Cike da kunya da fargaban abinda zai faru yace "Hajia dama na zo muyi magana ne." "Akan me?" Ta fad'a ba annashuwa a tare da ita, saida ya d'an k'ara sauta muryarsa yace "Akan Salma ne." Ba tare data kalleshi ba tace "Wace Salma fa?" "Salma ta tonton Sani." Da k'arfi ta juyo kanta ta kalleshi, cikin tsananin mamaki tace "Me kuma ya had'aka da ita? Meya faru?" Sunkuyar da kai yayi kafin yace "Hajia dama ni da ita muna soyayya ne, shine yanzu na..." "Ka me?" Yanda tayi magana da k'arfi tare da mik'ewa yasa kowa kallonta, saida ta gyara tsayuwarta tana fuskantarshi tace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _55_ "Junaid yanzu ma wani sabon rashin mutumcin ne ka zo min dashi? Ina ce kana d'aya daga cikin wanda suka fi kowa sanin bana buk'atar doguwar mu'amula tsakanin ahalina dana Inussa (yayan Alhaji), shine yanzu zaka zo min da wata banzar magana wacce k'arshe nasan zaka ce kana son auren jikarshi ne, to ban yarda ba kaji na fad'a maka, in kuma kace kaji ka gani to zan zuba maka ido a karo na biyu." Kallonta yayi yace "Kiyi hak'uri Hajia idan ranki ya b'ace, wannan karan a shirye nake dana miki biyayya, idan har baki amince na aureta ba zan hak'ura, dan ba zan k'ara sab'ama umarninki ba." Cike da zak'alk'alewa tace "To ban yarda ba, kaje ka nemi wata yarinyar ba dai wannan ba." "Shikenan Hajia." Ya fad'a yana barin falon, da kallo Ammar ya bishi har ya fita, tab'e baki yayi ya d'auki Ameera dake ta narke masa ya fice shima, ko da Amna taje ta same shi har ya shiga wanka, yana fitowa duk taga yanayinshi ya canza amma ba tace komai ba, yana shiryawa cikin k'ananan kaya ya sake d'aukar makullin mota ya zo kusa da ita ya sumbaci goshinta yace "Zan fita saina dawo." Cikin ladabi tace "A dawo lafiya." Da k'yar ya rabu da Ameer dake son saiya tafi da shi, yana fita ya d'auki hanya bai zame ko ina ba sai gidan Alhaji Inussa, ba laifi Alhaji anja shekaru ga kuma jiki da ake fama dashi, zaune yake kan kujera ko tashi baya iya wa sai an taimaka masa, hakan ne yasa Ammar jin ba dad'i sosai akan wofantar da zumuncin da akayi, dan sai yanzu da ya zo ake fad'a masa ya kusa shekara da wannan ciwon, tambayarsu yayi ya ake zaune gida dashi haka? Sai yayan Salma *Rashid* ne yake fad'a masa cewa "Ai har Niamey aka kaishi, amma sun ci ciwon ya riga daya tab'a zuciyarshi, magunguna dai aka had'omu dasu ana ta bashi, amma nan gida ma ana had'a mishi da maganin hausa." Kallonshi yayi yace "Ina takardun jinyar tashi?" Juyawa yayi ya kalli amaryar Alhajin yace "Hajia ina takardun suke?" Tashi tayi cike da manyantaka ta shiga d'aki, d'aukowa tayi ta kawo masa ta bashi, dubawa ya dinga yi kamar ba zaiyi magana ba yana nazartarsu kafin ya kalli Sani dake tsaye yace "Tonton ciwon nan na k'afarsa yana k'amari ne saboda maganin hausar da ake bashi, ciwonshi ya kai matakin da zai buk'aci zama kusa da likita, dan haka ku d'auke shi mu kaishi asibiti." Cikin jin nauyi Sani yace "Amma Ammar ai ba ayi haka ba, daka bari su yaya *Lawali* su zo sai muji ta bakinsu." Mik'ewa yayi tsaye yace "Dan ciwon ba'a jikinku yake ba ne zaku fad'i haka, to idan kun gama shawarar saiku same shi a asibiti na, ni zan d'auki nauyin komai da za'a mishi, amma ba zai sake kwana a gidan nan ba da ciwo." Rashid ya kalla yace "Kama shi mu tafi." Kama shi sukayi ya mik'e inda ya fara dogara sanda har suka fita, baya suka zaunar dashi sai Rashid dake gaba tare da Ammar, ko da suka je asibiti cikin gaggawa yake komai ya ware mishi d'aki na musamman, cikin k'warewa da salo ya fara bashi kulawar da yake buk'ata a lokacin, har magunguna saida ya canza mishi ya siyo a aljihunshi, lokacin daya kammala komai ya d'auki hanyar komawa gida dare yayi sosai, dan haka ko da yaje ya samu Amna ma har tayi bacci, bai takurata ba sai kwantawa da yayi tunani fal zuciyarshi. Washe gari ko da ya fito daga falon Hajia Amar ya gani tsaye ya kafe wuri d'aya da ido, bin wajen yayi da kallo sai yaga Farisa ce da k'annanta zasu tafi makaranta, tab'e baki yayi ya matso kusanshi ya dafa shi yace "Matsalar zuciya ce?" A d'an tsorace ya kalleshi sai kuma yayi murmushi yace "Kamar ya?" Saida ya kalli k'ofar gidan yace "Da alama akwai wani abu da kake ji, ko ba haka ba?" Matse bakinshi yayi cikin sanyin jiki yace "Kuskure ne, amma bai kamata na bari haka ta faru ba tun farko." Gyara tsayuwa Ammar yayi yace "Kuskure kamar ya? Soyayyar taka ce kuskure ko kuma wacce kake so ce bai kamata ka so ta ba?" Shima gyara tsayuwa yayi yace "Wacce nake so mana, kai fa kasan komai." Girgiza kai yayi yace "A'a ban sani ba, fad'a min miye matsalar?" Cikin nutsuwa Amar yace "Ammar kasan fa Hajia ba son doguwar mu'amula take tsakaninmu da Hajiarsu Jibril ba, sannan ina auren Umaimah wanda dukansu yan uwa ne, kaga abune da ba zai yiwu ba ai." Wani kallo ya masa kamar na wanda baisan ciwon kansa ba kafin yace "Yanzu Amar wannan har dalili ne da zai iya sawa ka hak'ura da wacce kake so? Hajia ba tana nusar damu dasu bane saboda Allah, tana so muyi nesa dasu ne saboda izzarta da wani buri na zuciyarta, hakan haka saika haramtawa kanka abinda Allah ya hallata maka." K'ara matsawa yayi kusanshi ya sake dafa shi yace "D'an uwa, daga ni har kai mun sani ba wai kowa ya auri wacce zuciyarsa ke so bane, umarninta ne muka bi mukayi biyayya, kada ka tauye kanka ta b'angaren abinda kake so in har ba sab'on Allah bane, idan kace zakayi haka kuma wallahi zaka wahalar da kanka ne sannan ka wujijjiga zuciyarka, idan bar Hajia tace bata yarda ba ka tambayeta dalili? Sannan ta fad'a maka hujjar k'in amincewarta." Nunfasawa yayi ya ci gaba da cewa "Kar kayi wasa da damarka yaro, inhar kana sonta to kawai ka fad'a a gida asan abunyi." Murmushi Amar yayi yace "Daga yanda kake magana d'an uwa kamar kai ma ka fad'a soyayyar nan ko?" Murmushi yayi shima yace "Sosai ma, amma ni dalili na da yasa na hak'ura da soyayyata yafi naka k'arfi gaskiya." Da mamaki yace "Kamar ya? Me yasa ka hak'ura da soyayyarka? Bansan da sarewa ba haka ma tsoro, na d'auka idan ka samu wacce kake so zaka tsaya ne wajen ganin ka same ta ko da hakan zai iya janyo yak'i." Cikin fad'ad'a murmushi yace "Amar wasu abubuwa basa buk'atar jarumta ko rashin tsoro, kai halal d'in bata haramta maka halal d'inka ba, karin maganar hausa ne da ake cewa wai *ana barin halak ko dan kunya*, ni tawa halal d'in ta haramta mani wata halal d'in ne." Wani kallo ya bishi dashi na son gano abinda yake nufi, shi kanshi saida ya ji bugun zuciyarshi ya k'aru da sauri sauri, cike da mamaki da tsoron abinda zai fad'a yace "Ammar, kar dai kace min kankana kake so?" Rintse ido yayi tare da buga tagumin rashin jin dad'i, ya jima haka kafin ya bud'e ido ya kalleshi, wata iska ya furzar mai zafi tare da d'aga kafad'u yace "Amna duniyata ce, uwar 'ya'yana ce, kwanciyar hankali na ce da farin ciki na, k'aramin abu idan ya gilma ta gaban rayuwata marar dad'i gurinta nake zuwa na samu nutsuwa, ba zan iya mata butulci ba har na bari tasan abinda ke zuciyata ba, Hamna kuma ita ce burin zuciya ta, abincin ruhina sannan mafarkina, su biyun sun sani tsakiya bansan ya zanyi ba, *sune k'addarata*, na d'auka da hannu biyu har naga yanda ubangiji zaiyi dani." Yana gama fad'a ya bar wurin, da kallo ya bishi sai yaji kamar ya zubar masa da hawaye, shima cikin k'warin gwiwa ya shiga wajen Hajia dan fad'a mata abinda ke ranshi babu b'ata lokaci, bayan sun gaisa yake sanar da ita shi fa yana son k'ara aure, cike da mamaki tace "Shalele aure kuma? Yaushe akayi auren naku da har zaka k'ara wani? Umaimar bata kwantar maka da hankali ne?" Cikin turo baki yace "Hajia kawai ina so na k'ara auren ne, dan Allah kada ki hanani." Girgiza kai tayi tace "Ba zan hana ka ba, amma fad'a min wace yarinya ka samu?" "Farisa." Ya fad'a ko kallonta baiyi ba, k'ank'ance ido tayi tace "Wai me yasa ba kwa ganewa ne yaran nan? Shalele ya zaka min haka? Wace Farisa kuma yarinyar da ko jinin al'ada yanzu ne ta fara shi." Kallonta yayi yace "Eh ita Hajia, a hakan ta min wallahi ina so." "Kayi hak'uri shalele ka nemi wata, ba zan yarda a sanadiyarku ba na rasa ji da kaina da d'aukakata ba." Kallonta yayi da matuk'ar mamaki, amma daya tuna abinda Ammar ya fad'a masa sai yace "Hajia d'aukakarki? Yanzu akan hakane zaki hana mu abinda zuciyarmu ke so?" Shiru ta masa sai kawai yace "To Hajia me yasa ba kya son aure na da ita?" "Saboda kakarta tsohuwar karuwa ce, ita kuma wannan rayuwa tana bin ahalina kamar yanda yan biyu ke bin mahaifa, a dalilin auren Farisa kana iya haihuwar yaran da zasu addabeka." Cikin jinjina kai yace "Hakane, na gani kam, to amma Hajia taya su tanti Zeinabu suka samu Junaid ta wannan hanyar bayan kuma hakan ba d'ab'iar zuri'arki bace? Ko dai zama da Hajiar..." Cak ya tsaya da maganarsa saboda hannun data d'aga da niyyar marinsa sai kuma ta tsaya, kallonshi tayi ido jawur kamar zatayi kuka ta nuna masa k'ofa tace "Fita, fitar min a d'aki." Mik'ewa yayi ya kalleta yace "Kiyi hak'uri Hajia, Umaimah ba irin matar da nake so bace, ba zan iya hak'urin zama da ita ba gaskiya har bak'in cikinta ya kashe ni, ki taimaka ki yarda da aure na da Farisa." Fita yayi ya rufe mata d'akin, zaune tayi kan gado ta fara wa kanta karatun tanutsu, wata rana fa komai zai iya fitowa in tayi wasa, to miye mafita daya wuce ta amince da buk'atarsu, take ta sawa zuciyarta ruwan sanyi ta d'auki niyyar gyarawa ko dan kar a mata dariya ma. *Da dare* ma kowa na harkar gabanshi ya wuce d'akin Ummy data kira shi a waya tace ya zo, da sallama ya shiga ya zauna yace "Ummy gani kince na zo." A hankalce ta kalleshi tace "Ammar, da izinin ka aje Baba Inussa a asibiti?" Kallonta yayi yace "Ummy kafin nayi taimako saina nemi izinin wani? Kawai naga yana buk'atar kulawar asibiti ne shiyasa na d'aukeshi." "Amma kasan hakan me zai iya janyowa kuwa? Me yasa baka tsoron abin fad'a ne?" Nisawa yayi yace "Ummy ba haka bane, kamar yanda zamu iya bayar da komai namu ga Alhaji matsayinsa na kakanmu haka shima Alhajin, wani k'aramin abune daya faru tsakaninsu shekaru da dama, mu bamu san komai ba bai kamata mu tayasu hura wutar ba." Cikin d'aga murya tace "Ammar, ina so ka sallameshi daga asibitin nan ka kaishi wata ko kuma ka mayar dashi gida ka ci gaba da bashi kulawar, amma zamanshi a asibiti zai janyo maka matsala da ma ni kaina, ni kuma wallahi ba zan yarda ka k'ara ja min banzayen matsaloli ba ina zamana lafiya." Kallonta yayi fuskarsa a had'e yace "Kiyi hak'uri Ummy, a gaskiya ba zan iya d'aukeshi daga nan ba, bugun k'irji nayi na nuna na isa dashi shiyasa na kawo shi nan, saboda tsoron Hajia kawai ba zan lalata aikin alkairin da nayi niyya ba, Ummy ke ma ya kamata ace kin rage tsoron nan da kike mata, tsoron Hajia yana saki kina aikata kuskure a kowane numfashi na rayuwarki." Tsuru ta masa da ido, gaskiya ne abinda ya fad'a fa, amma da yake abun ya gyauraya da jininta saita rufe ido tace "Naji ina tsoronta, kawai ina so ka d'aukeshi daga asibitin nan." Kallon mamaki ya mata yace "Hajia Alhaji ne fa d'an uwan Alhaji na Abbanmu, ya zaki ce a masa haka?" Cike da k'aguwa tace "To naji, idan ba zaka fitar dashi ba ka fad'awa Hajia tasan da zamanshi, kaga idan ta amince shikenan saiya zauna." Tashi yayi tsaye ya juya mata baya yana fad'in "Hajia dai, Hajia dai, wai abun alkairi ma saika nemi umarnin Hajia, to wai ita ta busa mana rayuwar nan ne ko me?" Mik'ewa Ummy tayi ita ma tace "Na sani dama ba zaka yi ba, ban isa na saka kayi ba saboda baka d'auke ni bakin komai ba, kaje kayi duk abinda kaga dama, amma ka sani shirme ko haukanka ba zai k'ara sani a damuwa ba, yanzu b'ace min a gani." Kallonta yayi yace "Ummy me yasa kullum sai ki kore ni daga wajenki? Kina yawan fad'a min b'ace min da gani, me yasa?" Cikin b'acin rai ta juya mishi baya tace "Saboda ban son ganin na ka." K'uri ya mata da ido yana kallonta ta juya masa baya, rintse ido yayi yana sauke numfashi yana son zuciyarsa ta kwanta, bud'a ido yayi har sunyi ja sosai jijiyar kanshi duk ta fito, dunk'ule hannunshi yayi ya daki bangon wurin, juya baya yayi shima a lokacin ta juyo da sauri, yana juyowa suka had'a ido yace "Ba kya son gani na? Ni d'an halak ne Ummy kuma mai biyayya, tunda har kika fad'a da bakinki ba kya son ganina zan miki nesa da kaina ta hanyar samar miki da farin ciki, amma duk da haka duk ranar da kika buk'aci na zo gareki zan zo da saurina, saboda ke mahaifiyata ce kuma ina son ki, *ina sonki sosai* Ummy." Fita yayi daga d'akin sai kawai Ummy ta durk'ushe ta fashe da kukan da bata san ma na miye ba. Shima yana fita bai kula kowa ba ya nufi b'angarensu, Amna na zaune cikin k'ananan kaya riga da wando sai yara dake wasarsu, cikin dakakkiyar murya yace "Ki shirya kayan yaran nan da safe zamu tafi Niamey." Zaro ido tayi ta bishi da kallon mamaki shi kuma kai tsaye d'akin shi ya shiga, kamar hauka haka ya shiga had'a kayanshi yana turawa a akwati, jin Amna ta shigo shi kuma baya so ya zubar da hawaye gabanta ko ya sauke hushinshi akanta yasa shi saurin shigewa ban d'aki, da kallo ta bishi cikin sanyin jiki ta kalli kayan da yake ta bankawa a akwati, a hankali ta shiga gyara zaman kayan tana saitasu, tsawon lokaci kafin ya fito yana ganinta ya sunkuyar da kai yace "Bana no ki aje min kaya, kije ki had'a naki dana yaran nan, idan kuma ba zaki tafi ba ke kika sani zan d'auki yarana." Da sauri tace "Amma yah..." Da k'arfi kamar zai tsaga d'akin yace "Amna bana son tambayar banza, kiyi abinda na fad'a miki kawai." Shagwab'e fuska tayi ta sake takowa zata matso ya sake daka mata tsawa "Amna ki fita ki bani wuri, bansan ganin kowa a kusa dani, bana so na sauke b'acin rai na akan ki." Da sauri ta sake takowa gabanshi tana fad'in "Na yarda ka huc..." Wani bazawarin mari ne ya d'auke fuskarta dashi da yasa ta fad'awa kan gado da k'arfi ta kifa gaba d'aya, rintse ido yayi dan har cikin ranshi yaji marin, cikin hushi da fad'a yace "Na fad'a miki kiyi nesa dani, wai ke ba kya fahimta ne? Ki dinga yin nesa dani kamar yanda kowa keyi mana, yanzu gashi kinsa na mareki a banza." Juya baya yayi da k'arfi yana dafe kanshi, cikin rawar jiki na bala'in marin data sha tana karkarwa ta mik'e, cike da k'arfin hali ta rik'o hannunshi ta juyo dashi gabanta, suna had'a ido ta fashe da kuka tana shafa kanshi ta ko ina tana fad'in "Dan Allah yah Ammar ka daina, tsorata ni kake idan kayi irin hushin, bana so ka daina kaji, na yarda ka huce a kaina amma karka cutar da kanka ko wani, dan Allah kaji." Tsakiyar idonta yake kallo sai yaji hawaye na fitowa a idonshi, cakumarta yayi da k'arfi ya matse yace "Me yasa Amna? Me yasa Amna?" Kuka kawai take har da ajiyar zuciya, jawota yayi jikinshi sosai ya rumgumeta, tun yana yi a hankali har ya fara saka k'arfi yana matseta sosai kamar zai mayar da ita ciki, duk da tana jin zafi amma haka ta daure, sun jima haka kafin ya d'ago ba alamar annuri ya saketa ya juya zai bar d'akin, da sauri ta rik'o hannunshi tace "Ina kuma zaka je?" A hassale yace "Yaro ne ni Amna da sai kin tambaye ni inda zanje?" Girgiza masa kai tayi tace "A'a, amma ba zan barka ka fita a halin nan ba yah Ammar, idan ka fita ranka a b'ace zaka iya yin komai." Tsabar neman fitina saiya rufe ido yace "Amna ni? Mahaukaci dama kike kallona ban sani ba, eh lallai yau ta tabbata kowa mahaukaci yake d'aukata." Cikin zubo da hawaye ta girgiza masa kai alamar a'a, k'wafa yayi ya juya zai fita ta sake rik'e hannunshi, fizgewa yayi da k'arfi zai bar d'akin ta tare gabansa da gudu, rufe k'ofar tayi cikin kuka tace "Wallahi babu inda zaka je, nasan halinka yah Ammar in dai har ka fita yanzu saika nemi wani da masifa, ka bigeshi ko ya bigeka shine burinka, dan haka na zab'i ka zauna tare dani in ya so ni ka kashe ni, amma hankali ba zai kwanta ba dan bansan da wa zakayi rigima ba." Belt d'inshi ya fara zagewa yana fad'in "Shikenan, bari na fara miki laga-laga sai na bi ta kanki na wuce." Matsowar da yayi kusanta da sauri yasa tayi saurin duk'ewa tayi k'asa tana jingina a jikin k'ofar, yana ganin ya saki d'amarar cike da tausayinta ya sunkuya ya kamota, bud'a ido tayi ta kalleshi saiya rumgumeta yace "Amna baki da hankali ko kad'an." Saida ta rumgume shi sosai tace "Na sani yah Ammar, shiyasa nake so ka dinga saita ni." Tallabo kanta yayi ya had'e bakinshi da nata ya shiga tsutsa, shiru komai ya kwanta aka shiga wata duniya, ta d'auka an bar maganar tafiya ashe ko kad'an, cikin muryar bayar da umarni ya nuna ta yace "Ki tabbatar kin had'a kayanki dana yaran nan." Kallonshi tayi, ba zata iya magana ba yanzu kam dan zasu sake samun matsala, sai kawai ta bishi da to da niyyar yin sun tafi ta lallab'a shi tasan meya faru haka. *Washe gari* da sanyin safiya suka fito a shirye, ko falon Hajia bai shiga ba yace Amna dai taje ta fad'a musu zasuyi tafiya dan kar aga basu nan, haka ta shiga jiki a sanyaye bayan ta gaishesu ta fad'a musu, kowa yayi mamaki amma tunda tace tare dashi ne sai aka bisu da addu'a kawai, tare da Hamna suka fito suka tsaya farfajiyar gida inda suke iya hangenshi tare da yaran a mota yana jiranta, tsaye suke suna sallama inda Hamna ke d'agawa yaran hannu, idonshi na kanta ya fito da wayarshi, sak'o ya rubuta ya turo mata yana ci gaba da kallon fuskarta. Tana jin wayarta tayi k'ara ta fito da ita ta duba, kallonshi tayi ta kuma kallon wayar, sak'o ne ba mai tsayi ba, amma ma'anarshi da abinda yake nufi da kuma yanda ita ta fahimci sak'on yayi kusa ya tsayar da tafiyar jinin jikinta, kad'an ne ya rage bata iya nuna abinda ke ranta ba, kafe wayar tayi da ido tana sake maimaita karanta sak'on mai d'auke da wasu tsirarun kalmomin kamar haka _"Bansan me yasa ke da Ummy kuka tsane ni ba, amma zan tafi nayi nesa daku dan na hutar da zukatank'u."_ Suka tsaneshi fa yace, shin yasan me take ji a zuciyarshishi a game da shi kuwa? Bai sani ba, Amna dake kallonta ne tace "Yer uwa ko zamu tafi tare ne dan kar kiyi kewata?" Cikin gigita, cikin rashin sanin madafa, cikin hargagi da son fitar da abinda ke ranta, cikin yanayin da bata san tayi magana dashi ba, yanayin da bata tab'a ma yer uwarta magana ba sai gashi yau dalilin *namiji* ta mata, tsawa ce mai ban tsoro ta mata ta hanyar fad'in "Ba zanje ba malama ki rabu dani, kiyi rayuwarki nayi tawa, duk ke ce silar komai." Tana gama fad'a ta taka da sauri ta nufi motar, ta tafi da niyyar yin wani abu daban, amma Ameer na lek'o kanshi ta mota ta sauke ido akan yaron sai taji ta rasa kuzari da k'arfin halin, sai kawai ta juya ta nufi inda motar ta take da sauri. Amna da tayi mutuwar tsaye odar daya mata ce ta farfad'o da ita daga doguwar sumar, da k'yar ta iya d'aga k'afarta ta shiga motar suka fita daga gidan, saida ta ga fitarsu da wasu mintuna kafin ta fita ita ma tana kuka. *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _56_ Ammar dai ya tafi tare da iyalinshi, inda suka kwana biyu a garin Niamey a masaukin da mahaifin Amna ya tanadar musu, a kwana na uku ya gama musu shirin komai har da allura saida aka musu na shiga wajen k'asarsu, ticket ya cirar musu ya aje motarshi anan gidan suka tafi *cotonou*, a kwanakin da sukayi saida yayi magana da abokinshi likita wanda ya yarda da k'warewarshi kan ya ci gaba da duba mishi Inussa, sannan duk abinda ake buk'ata a mishi magana zai bayar, sun isa lafiya kuma da yake harka ce ta dala ya samu masaukin daya dace da tsarinshi da kuma iyalinshi, sun fara rayuwarsu kamar yanda suke yi a gidan, amma anan kullum zai fita waje sai Amna tace ya kula kar ya ja musu rigimar da za'a k'onasu da ransu, shi kuma abinda yake fad'a mata shine "Amna ke ma mahaukaci kike d'aukata, amma ba komai zan kiyaye ko saboda ke." *A gida* fa abubuwa sun shiga juyin waina inda komai ya fara tafiya a hargitse, Hajia da kanta tace ta amince da auren Junaid da Salma, sannan ta bawa Amar dama ya nemi auren Farisa, ta b'angaren Junaid anyi matuk'ar farin ciki ganin zumunci zai had'u tanan wajen, amma a b'angaren Amar tashin hankali ne ya kunno kai daga wajen Umaimah, dan kuwa ranar da taji labarin saida ta mata dukan tsiya har cikin falon uwarta, hakan ya b'ata ran Amar yace ta je gida kawai saiya neme ta, Alhaji ne ya bashi hak'uri yace ya lallab'ata kishi ne, Zeinabu ma hak'uri take bata dan ita yanzu ta nutsu tun abinda ya faru, amma Umaimah sai botsarewa take wai akan me zai mata kishiya kuma k'anwarta data yarda da ita har take shiga d'akin baccinshi. Saboda gudun matsala yasa Soueiba da Labaran cewa in akwai matsala kawai a bari, Hajia tace ai bata isa ba Umaimahr banza ko uwarta bata isa ta hana auren ba, Farisa aka tambaya idan tana so to babu fashi, abinda ta fad'a kawai shine "Ni karatu nake so nayi." Hakan yasa Amar d'aukar alk'awarin barinta tayi karatunta har aiki ma udan tana so, magana ta kankama sosai har anyi komai an gama an saka rana. Duk da akwai mutane a gidan kuma ana hayaniya, amma kowa ya tabbatarwa da kanshi akwai mutum d'aya da babu a gidan, babu nishad'i ko wata raha, Hajia Alhaji da Ummy abun yafi damunsu fiye da kowa, ko kiransu a waya bai cika yi ba saiya kwana biyu, yanzu Hajia saita wuni ta kwana a kujerar nan zaune bayan gaisuwa babu wanda zai tsokaneta ko ya sakata dariya ko nishad'i, idan abinci ake ci haka kowa zai gama ya tashi, inba tashin hankali ba na auren Amar ko kuma sab'ani na zaman tare baka jin komai a gidan, dan haka yanzu kowa ya zama shiru zaman d'aki yafi yawa, kowa saiya had'a kan yaranshi k'ananan ya shige d'aki ya zauna abinshi, har Zeituna ma dake da yarinya d'aya, sai dai ita suna waya da Ammar kullum dan yana girmamata sosai. Hamna ma gaba d'aya ta canza kamar ba ita ba, jikin nan nata duk ya rage yanzu sai lalacewa take, tafi son zama wajen aikinta fiye da ko ina, idan ka ganta gidan nan da dare ne, kuma gari na wayewa zatayi sammako ta fita, hatta Shureim yanzu ta rage kusanci dashi kamar da, sai dai tana waya da Amna akai akai suna gaisawa, wani lokaci haka zata tashi tayi ta b'ata rai a banza, a haka ita ma rayuwar ta godewa Allah kawai zata ce. *A kwana a tashi* ba wuya a wurin Allah, sai gashi an sake d'aura auren Junaid da Salma da kuma Amar da Farisa sai Jamil da amaryarsa *Zeinab* shima, amare sun tare sun fara rayuwarsu mai cike da jarabawa, tunda akayi bikin aka gama Umaimah ke hushi da Amar bata kula shi, har ranar girkinta ya zagayo da safe ina abin kari tace ai bata dafa dasu ba, banza ya mata ya fita da rana ma bai dawo gidan ba, da dare ma daya tambayi abinci tace yaje amaryarshi ta bashi, murmushi ya mata ya fita daga d'akin, yana zuwa ya samu amaryarshi kam ta mishi dubaru ya cika cikinshi, ko da ya dawo bai kulata ba ya kwanta shima. Washe gari ya bata kud'i haka ma Farisa yace tayi girki, lokacin da take aiki a madafa Umaimah ta dinga masifa akan me zata karb'e mata ranar girki, ita dai bata ce komai ba saboda tana tsoronta. _Yan uwa rayuwa wata aba ce dake tattare da k'alubale da shubuha, wani lokacin zata iya zuwa maka yanda kake so, wani lokacin kuma ta zo da sab'anin haka, ka yarda ka karb'a ko kuma ka kafirce mata ya rage naka, so da dama mukan so abinda ba alkairi bane a gare mu, haka ma sau tari mukan fifita tsana ga wanda yake alkairi gare mu, shiyasa a kullum ya kamata kayi fatan zab'in Allah._ *Daren yau* duk suna zaune ana cin abinci Jamila ta shigo da gudu wai Umaimah suna fad'a da Farisa sai dukanta take, da gudu kowa yayi b'angaren nasu suka same su, tsaf tayi zaune kan yarinyar mutane tana mai k'aramin ciki tana bugu, ba tsayawa komai colonel ya d'auketa da mari, da k'arfi yasa k'afa ya turata tayi baya yana fad'in "Jaka kawai, yaushe haukan naki yayi tsanani har haka?" Lieutenant ne ya rik'e shi yana fad'in "Ya isa dan Allah karka ji mata ciwo." Tana mik'ewa Hajia ma ta kwad'a mata mari tana fad'in "Mahaukaciyar ina ce? Baki san halin da take ciki bane da zaki mata wannan dukan? Jaka ce aka kawo miki?" Tsayuwar rashin mutumci tayi tana ta wani girgiza da gunguni, Ummy ce ta kama Farisa ta shiga d'aki da ita tana dubata, Hajia kuma kallon Umaimah tayi tace "Bari Amar d'in ya dawo kiga yanda zanyi dake, wallahi sai kin shiga taitayinki." Wani par-par tayi da ido tana motsa baki tana fad'in "Ya dawo d'in a sa ya yanka ni sai me?" Wani mari colenel ya sake datsa mata a kumatu wanda yayi sanadiyar gabcewar jini daga hancinta da bakinta, duk'ewa tayi rufe da bakinta ta fashe da kukan da ko sauti babu tsabar azabar marin, cikin bala'i yayi kanta zai sa mata k'afa yana fad'in "Dan ubanki uwar tawa kike fad'awa magana? Sa'arki ce Hajia ko nine kika raina?" Da sauri lieutenant ya rik'eshi, jinjina kai Hajia tayi kawai ta fita a d'akin, bayanta suka bi sai ita da aka bari tana kuka, suna shiga falon akayi cirko cirko ana kallon Hajia data sunkuyar da kai, Alhaji dake zaune anan bai tafi ba dama ya tambaye su lafiya, kafin wani yace wani abu Hajia ta d'ago cikin dattako tace "Ba komai, zanyi maganinta." Tana fad'a ta mik'e ta nufi kan teburin cin abinci ta zauna, kowa cikin nutsuwa ya je ya samu kujera ya zauna, Zeituna da Zeinabu ne suka zuba abincin suka aje ma kowa gabansa, amma abun shiru babu armashi kamar anyi mutuwa, Hajia ce ta d'ago kai ta kalli kowa sai kawai tayi murmushi ta tangale hab'arta da bayan hannunta tace "Hausawa sunyi gaskiya da suka ce *duk wanda ya tuna bara baiji dad'in bana ba*, tabbas mutum baya sanin abinda yake so sai ya rasa wanda yake hannunshi, *Ammar* yana raye amma yau ranar yabon ta zo, duk da wani mawak'i yace wai *kar Allah ya kawo ranar yabo*." Nunfasawa tayi ta d'auke tagumin tace "Dukanmu anan mun sani da yana gidan nan a irin wannan lokacin da yanzu yasa kowa dariya koda kuwa tnda fad'in wata magana ne wacce mu zamu kalleta a rashin kunya ko fitsara, ko da bamuyi dariya ba akan shirmenshi zai zamana zuciyarmu bata tunanin damuwa, amma yanzu gashi rashin shi yasa kowa abinda ya ga dama yake yi." Saida ta sake kallon kowa tana murmushi tace "Yana son kowa a gidan nan, yana tsayawa kan matsalar data shafi kowa, yana da kirki da kuma d'ab'iu masu kyau." Dariya tayi ta kalli Alhaji da Husseina tace "Sai yanzu na fahimci dalilin da yasa tsofaffin gidan nan bamu da hawan jini, shine maganin ashe bamu fahimta ba tun wuri." Dariya sukayi a hankali sai Alhaji da yace "Ni nasan wannan ranar tana zuwa, kune kuka kasa fahimtarshi, amma yanzu gashi kuna fad'a da bakinku." Cikin sanyi murya tace "Kullum mukayi waya dashi ina tambayarshi yaushe zai dawo? Amma yanda na fahimta kamar bai saka ranar dawowa ba." Kallon Ummy tayi a raunane tace "Sa'ada dan Allah ki kira shi ki ce masa ya dawo, ya zo ko naji dad'i." Kallonta Ummy tayi tana tunani, sai kuma tayi murmushi tace "Hajia ke ma baiji maganarki ba ya dawo bare ni." Murmushi Hajia tayi ta kalleta tace "Ko yaron da bai mallaki hankalinsa ba yasan Ammar yana fifita soyayyarki kan ta kowa, duk yanda zai rud'e ya birkice ya fara sababi idan kika masa magana yana ji, ko hankalinshi ya gushe saboda b'acin rai indai zaki masa magana to zai bari." Kafe Hajia tayi da ido inda wasu kalamanshi suka dinga dawo mata a kai, da jimawa ya tab'a fad'a mata cewa "Ummy na so barin gidan nan tun a waccen lokacin, amma saboda tunanin halin da zaki shiga yasa ban tafi ba, ina tsoron na barki Hajia ta dinga takura miki." Sai kuma ranarta ta k'arshe dashi da yace "Amma duk da haka duk ranar da kika buk'aci na gareki zan zo da sauri na, saboda ke mahaifiyata ce kuma ina sonki, ina sonki sosai Ummy." Wannan tunanin data tafi yasa bata san har sun tashi daga zaman ba, Zeituna ce kawai ta rage a wurin tana kallonta, suna had'a ido suka sakarwa juna murmushi, cikin ladabi Zeituna tace "Gaskiya Hajia ta fad'a Ummyn Ammar, yana d'aukaka lamarinki fiye da komai, duk da rashin kulawar da kike nuna masa baisa ya tab'a yin hushi dake ba, duk yanda yake ganin darajata idan ya kirani kafin mu gaisa saiya fara tambayata ya Ummy take, saina tabbatar masa da kina lafiya kad'ai zai iya gaishe ni, aunty na fad'a miki a baya kuma yanzu ma zan maimaita miki, Ammar so da kulawarki kad'ai yake buk'ata, duk abinda yake yi wanda ba kya so kuna zama dashi cikin sauk'i zai daina." Ita ma barin wurin tayi suka barta, ta jima nan zaune tana tunanin abunyi kafin ta koma d'akinta. Hajia ma na d'aki Hamna ta sallamo, amsa mata tayi ta bata izinin shigowa, cikin sanyin jiki ta k'araso cikin ladabi tace "Hajia dama na zo neman alfarmarki ne?" Kallonta tayi ta aje wayarta gefe tace "Wace irin alfarma Hamna?" Cikin nutsuwa tace "Hajia dama su aunty *Hana* ne (k'anwar mamansu) zasu tafi Niamey bikin *Abdu*, shine nace zan tambayeki idan kin amince ina so mu tafi tare dasu?" Murmushi ta mata tace "Ba komai Hamna, kuje Allah ya tsare, a kula sosai kinji." Saida ta sunkuya tace "Nagode Hajia, insha Allahu." Da kallo ta bita har ta fita, har zuciyarta yanzu kam ta fara tausaya mata, sam babu maganar aure a sabgarta, samari da masu mata suna gosulo a k'ofar gidan akan ta, amma kowa sai tace bai mata ko ta kushe shi dole a rabu da ita, ita kuma bata so ta fitar mata da miji a yanda yanzu ta k'ara mallakar hankalinta take rik'akk'un shekaru ga kuma wayewa da karatu ba lallai ta yarda ba, sai dai kawai su ci gaba da addu'a Allah ya fito mata da miji ita ma tunda gashi har k'annan baya suna aure suna barinta. D'akin Ummy ta wuce ta fad'a mata zata tafi amma fa zata jima gaskiya, Allah ya tsare ita ma ta mata kafin ta fito, tsaf ta shirya kayanta wayewar gari kawai take jira. Tsakanin mata da miji ance sai Allah, Amar da ake tunanin d'aukar mataki akan Umaimah shi kuma ko da yaga jinin da take zubarwa sai kawai tausayinta ya lullub'eshi, (😂 auren kenan) sai ga Amar ya rarrasheta kan tayi hak'uri dukan da tonton ya mata, ko nasiha bai mata ba na abinda tayi, saida ya gama ita ma amarya Farisa ya lallab'ata yace tayi hak'uri. Da safe saida aka had'asu aka ja kunnensu sosai tare da tsorata ta hanyar fad'a mishi inta sake yayi duk abinda ya dace. *Bayan wata takwas* Ko da ya kira gida cikin farin ciki ya sanar dasu Amna fa ta haihu, abun farin cikin kuma shine ta sake haihuwar 'yan biyu duka maza, duk da basu gari amma gidan haka aka dinga murna da farin ciki, dan dama ana cikin hidimar haihuwar Zeinab ne Farisa kuma har tana da sati biyu da haihuwa. Ranar suna ko da ya kira yace an yi wa Alhaji da Alhaji takwara, ma'ana *Suleiman* da kuma *Yunus*, wannan abu ya ma kowa dad'i na wannan iyali, babu wanda ya tab'a tunanin a familyn Hajia kuma Ammar zai iya saka sunan Alhaji Inussa, dangi daga masu kiransu da Alhaji sai mai kiransu Baba, amma shi ya musu alkunya da *Abba* da kuma *Imam*, daga Niamey Hamna ta kirasu ita ma tayi musu barka, wqcce ita ma har yanzu tana can bata dawo ba tayi zamanta, musamman data tafi da kayan aikinta hakan yasa acan ma bata zauna ba, babu inda bata zuwa yin kwalliyarta, dan shiga gidan yana wuya saboda tsaro. *Shekara d'aya* Rasuwar Alhaji Inussa ma bata dawo dashi ba, Zeituna ta haihu Jamila Umaimah duk sun sake haihuwa, lieutenant ma ya saka masa ido ya dawo ko ya zauna can duk d'aya, amma Hajia ta damu sosai da rashin dawowar har ta fara fad'a tana cewa akwai abinda aka masa, kullum ya kirata sai dai ya mata shirmenshi ya mata kalaman soyayya yace mata zai zo idan lokaci yayi, ana haka Alhaji ya wayi gari babu lafiya, mutumin da bai tab'a ciwo ba, hakan yasa yanzu ko da ya kwanta sai abun ya masa kwaf yayi yawa, dan farko ma da aka d'aukeshi aka kaishi asibiti baisan halin da yake ciki ba, a ranar hankalin kowa ba kwance ba, asibiti kuma sun ce ayi gaggawar kaishi Niamey, Gambo ne ya turo jirgi musamman tare da lieutenant da Hajia suka tafi dashi, sai colonel da suka samu acan garin, saida aka kwana biyu Ammar yasan abinda ke faruwa, a ranar shima ya shirya ya taho hankali a tashe. Asibiti ya wuce kai tsaye a taxi, colonel kad'ai ya iya kallonsa yace "Ammar kai ne? Yanzu ka shigo garin?" Idonshi akan Alhaji dake kwance ido rufe duk jikinshi na'ura ce yace "Eh kawu, ya jikinshi? Me ya same shi ne?" Kafin yayi magana Hajia ta fad'a kan kafad'arshi tana kuka, hannunshi ya d'ora bayanta yana shafata yana fad'in "Ya isa Hajia ta, ban sanki da raguwar zuciya ba fa, ko kin manta ke ce kakata?" D'agowa tayi tana share hawaye da gyalenta tace "Tsoro nake ji Ammar, mutuwa karta rabani da Alhaji na, har yanzu ban nemi gafararsa ba." Kallon lieutenant yayi da colonel sai kawai suka mishi alamar ya fita da ita, a hankali yana rumgume da ita ya jata suka bar d'akin, a k'ofar d'akin suka zauna kan kujera ta k'arfe mai sulb'i kamar zaiba, rik'e yake da hannayenta yace "Hajiata, kiyi shiru ki daina kukan to, babu abinda zai same shi zai tashi, taya ma zai tafi ya barki bayan shekarun da kuka d'auka, ai ke dashi mutu ka raba ne." Kallonshi tayi cikin wani kukan tace "Kana cewa ba zai barni ba kuma gashi kace sai mutuwa ce zata raba mu, to idan fa lokacinta ne yayi?" Saida ya k'ara matse hannunta sosai yana kallon k'wayar idonta yace "Hajia, ke da Alhaji kun ci nasarar rayuwa, kun zo duniya kun rayu tare da iyayenku, kun girma kuka rayu da 'ya'yanku cikin gata da kulawa, sannan yanzu kuna tare da jikoki da yaran jikokinku, kun ci ribar rayuwa sosai, ku godewa Allah daya baku arzik'i na gidan duniya, wasu sun rayu da kud'i babu 'ya'ya, wasu sun rayu da yara babu kud'i sanadiyar talauci yasa yaran fad'awa mummunan rayuwa, wasu kuma ya basu komai kamar ku, Hajiata, a familynki babu irin mai matsayin da babu, colonel na soja, kina da lieutenant na douanes, kina da babban k'usa a cikin siyasa, kina da babban professeur da da likita, kina da ma'aikacin ga wanda yake karantar shari'a, ga k'anwarmu dake son zama yar sanda, ga mai kwalliya ga yar kassuwa ga wacce ke son fitowa a alk'ali, sannan ga k'aramin k'ananmu wanda tun yanzu ya zama ustaz kuma yake burin zama babban malami da dai sauransu Hajia, kuma duk k'ok'arinku ne ya janyo hakan, ni kam Hajia me zaisa kuyi bak'in ciki ne a sanda zaku bar duniyar nan wacce ko ba dad'e ko ba jima dai sai an barta." Kallon idonshi tayi sai kayi ta saki murmushi, ita ma rik'e hannunshi tayi sosai tace "In fad'a maka gaskiya Ammar?" Kai ya d'aga mata alamar eh, cikin rad'a tace "A gaskiya da bana son mutuwa ko kad'an, amma yanzu daka tunasar dani yawan zuri'ata da kuma matakai na rayuwa da suka taka a rayuwarsu sai naji ko yanzu na mutu banda damuwa, saboda nasan ko ba dukanku ba dole zan samu tsirarun da zasu bini da addu'a ta alkairi." Murmushi yayi sosai tare da sakin hannayenta yace "Bari na duba jikin Alhajin." Jinjina kai tayi ya shiga ciki, Alhamdulillah kam jikin a lokacin yayi dama, sai dai dukansu babu mai tunanin su bar wurin nan da Alhaji, dan kuwa su manya ne sun san komai shi kuma Ammar likita ne yasan yanayin, yanda suka ga Alhaji yayi yasa duk suka sare da al'amarin, tubarkallah wani kyau ne aka zubo mishi yayi jawur dashi, ga kumburi da k'afafunsa sukayi, haka dai daya farka suka sha hira shi da Ammar har da dariya sukeyi, da dare iyayen sun fita sai Ammar da Hajia zaune, da hannunshi ya bashi abinci yana idawa ya aje plate d'in, har zai kwantar dashi sai kuma yace "Alhaji zauna ka ci gaba da kallon Hajiarka, na yau dai kawai na danne kishina." Dukansu murmushi sukayi sai Alhaji daya kamo hannunshi yana sauke numfashi, saida ya saisaita nutsuwarsa da numfashinshi kafin yace "Ammar, dan Allah ku kula da kanku sannan ku rik'e zumunci, kai ne babba a yaran nan ka zama mai tsayawa kan lamuransu, Ammar ka rage zuciya da saurin hushi, sannan ka ci gaba da biyayya wa iyayenka, sannan ka..." Sai kuma yayi shiru, dukansu ido suka sakar masa hakan yasa yayi dariya ya kalli Hajia yace "Ka kula min da Hajia Zeeya'atu na, kakar nan taka babu wanda ya iyata sama dani, ni ne mijinta anan kuma ni zan zama mijinta a lahira ma, ta dace dani, nima kuma na dace da kayata." Cike da tabbatarwa yace "Insha Allah zanyi Alhaji." Yanda ya k'arashe yana dariya yasa Hajia fashewa da kuka, d'ora kanta tayi kan k'afafunshi dake mik'e, dafa kanta yayi yace "Bana son ganin kukanki Zeeya'atu, ki daina kinji karki sani kuka nima." Ba tare data d'ago ba cikin kuka tace "Tun bayan rasuwar iyayena a bakinka kad'ai nake jin sunan Zeeya'atu, Alhaji bana so na daina jin sautin nan, ka ci gaba da kirana haka dan Allah, hakan zaisa naji a raina akwai mutum d'aya daya isa dani kuma yake da iko a kaina." Kallon Ammar yayi sukayi murmushi, k'ara shafa kanta yayi yana fad'in "Zeeya'atu na, Zeeya'atu na ki daina kuka kinji, bana son ganin hawayenki Zeeya'atu." D'agowa tayi ta kalli tace "Zan iya yanzu Ammar?" Fahimtar inda maganarta ta dosa yasa shi d'aga mata kai yace "Yanzu ne lokacin daya dace Hajia." Jinjina masa kai tayi sannan ta kalli Alhaji, a hankali ta mik'e daga kan kujerar ta tureta baya, *me zai faru? Wace rana ce yau? Wane babban tarihi ne haka?* Hajia Zeeya'atu da kanta ce k'asa akan gwiyoyinta biyu a gaban Alhaji Suley, ko kuma nace muku Suley, hawaye a idonta cikin nadama da neman yafiya ta k'ara fashewa da kuka tace "Ka yafe min Alhaji na, ka yafe min dan Allah ba dan halina ba, in dan halina ne wallahi ko kallo ban isheka ba, na muzguna maka a rayuwa, na cutar da kai fiye da kima, na wulak'antaka na tozarta darajarka ta d'an adam, na ci zarafinka tare da yaga rigar mutumcinka, na yi wasar kura da rayuwarka, na..." Hannunta ya rik'o da sauri yace "Zeeya'atu, ya isa haka kinji, na yafe miki duniya da lahira, Zeeya'atu ban tab'a rik'eki duk abinda kike min ba, da farko ina miki uziri da d'aga miki k'afa saboda hallacin mahaifinki gare ni, amma daga sanda na bud'a idona naga duk girman gidan nan a cike yake da mutane, kuma kaso biyu daga cikin uku duk ke ce tushen samuwarsu sai kawai naji na k'ara k'aunarki, sannan naji na yafe miki komai da kika min, dan haka karki damu kan wannan Zeeya." Kallonshi tayi sai yace "Tashi dan Allah kar yaran nan su shigo su ganki haka, sai kisa su d'aureni na gurfanar musu da uwa, kinsan fa babu muk'amin da babu a 'ya'ya da jikokinki." Cikin turo baki na shagwab'a ta mik'e tana fad'in "Ai da kai da kaya duk mallakar wuya ne, kuma sun samu matsayin da suka samu ne saboda samun jajirtaccen uba kamar ka." Saida ta zauna ta kalli Ammar tace "Na fad'a maka dama shi d'in na musamman ne, hak'uri ne dashi kamar damo." Dariya sukayi sai Alhaji daya mata wani kallo yace "Ke kuma akwai hauka a kanki Zeeya." Dariya Ammar yayi yace "Hum! Ashe gado nayi, shiyasa har matata ke min kallon mahaukaci." Dariya Alhaji yayi sai Hajia data mishi dak'uwa, hannu Alhaji ya mik'awa Ammar ya rik'e gam yana murmushi yace "Ko mutuwa ta zo min yanzu babu sauran k'unci a tattare da zuciya ta, kana tare dani ka min alk'awarin kula da yan uwanka, sannan yau Hajia ta nemi affuwata, alamu ne na ta d'auki hanyar gyara halayenta marasa kyau, hakan ya sani farin ciki, zan tafi gidana na gaskuya ba tare da tunanin zata ci gaba da takura kowa ba, ta mulki yaran kuma tana so ta mulki jikoki, abu ne ba mai yiwu ba, shiyasa ina jiye mata ranar da zata fara kuka kan rashin cikar burin da wani baiyi ba, Alhamdulillah Allah." *Da asuba* mazan duk sun tafi masallaci sai Hajia a d'akin tayi sallah, a hankali ta d'ago kai ta kalleshi kwance ido rufe, ta d'anyi mamaki jin bai nemi ta taimakasa ya tashi yayi alwala ba, dan ko ranar da suka zo jikin ma babu dad'i saida aka tayar dadhi yayi sallah, ci gaba tayi da jan carbinta har zuwa wani lokacin, da sauri ta juya jin n'aurar nan ta canza k'ara daga yi d'aya bayan d'aya zuwa da sauri babu k'akk'auci, sam sai bata damu ba kawai ta ci gaba da abinda take, suna shigowa suka shiga kallon n'aurar suna kallon juna, Ammar daya kafe shi da ido ne ya d'an matsa kusan gadon, wani kallon tsoro ne yake masa har saida ya kamo wuyan hannunsa ya rik'e yana sauraran harbawar jijiyarshi, da sauri ya juyo ya kallesu ya musu alama da su fitar da Hajia waje, colonel ne ya d'an fita saiya lek'o yace "Hajia ana magana." Tashi tayi ta fita sai Ammar daya shiga duba Alhaji yana kallon n'aurar dake haska bugun zuciya dana numfashi, dafe hannayenshi yayi kan gadon yana sauke numfashi, lieutenant ya matso yace "Ammar." Saida ya sake furzar da iska ya d'ago idonshi sunyi ja ya kalleshi, cikin amon murya mai gindayarwa yace "Bari na dubo likitocin." Ya taka da niyyar fita saiga docteur ya shigo d'akin, zaune yayi yana kallonshi shima yana duba shi, a hankali kuma saiya shiga cire mishi duk wasu wayoyi da abinda aka mak'ala mishi. *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _57_ Mutuwa mai raba tsakani, sun d'auka Hajia zata iya ja musu matsala ita ma, amma sai tayi juriyar da basuyi tunaninta ba, kasancewar Alhaji babban mutum yasa cikin k'ank'anin lokaci mutuwarshi ta zaga garuruwa da dama, an shirya kaishi gidanshi na gaskiya a Maradi, dangi sun jijjiga anyi kuka kamar ba za'a tsagaita ba, magana d'aya ce ke fita daga bakin kowa ita ce "Alhaji akwai hak'uri, ga faran faran da kowa, ga hira idan kuka zauna dashi babu ruwanshi sannan ga alkairi." *04:30* na yamma jirginsu ya sauka, a filin jirgin aka taresu daga can zuwa mak'abarta, a wannan rana kuma a wannan lokaci duk wanda ya fito da niyyar zuwa wani wurin kuma ya had'u da motocin yan rakiyar nan, to fa dole ya tsaya ya gyara zama dan in mai saurin bacci ne ma saika fara gyangyad'i kafin ka iya wuce, mutune dai ba wata tsiya ba kace duka garin ne aka taru, mutane har saida suka koma kallon al'ajabi ba wai jimamin mutuwar ba, babu motar da babu a taron nan, idan aka wuce sai kaji kamar k'asa na girgizawa saboda rubdugun mutane, ance alamun kyakwayan k'arshe ne jama'a ma, sai dai fatan dacewa kawai amma ta wannan b'angaren Alhaji ya cinyesu har ma da d'oriya akai, hakan ma dan wasu suna wasu garuruwa basu samu halarta bane. Gidan mutuwa ya zama kamar gidan biki, wannan jimami daga sanda aka kwantar da bijimin sa aka yanka aka shiga kiciniyar sarrafa shi, sai ga mata sun d'ora guma guman tukane na d'ori tare da girke buhun albassa ana ta yankewa, abu fa yayi k'amari sam kamar ba mutuwa bace a kayi, jimamin dai anbar na kusa dashi suyi, amma hira ta b'arke tsakanin mutane hira kuma ta duniya, ko da rana tayi aka dinga raba abinci da nama har ka ci kayi guzuri dashi, b'angare d'aya kuma masu karb'ar gaisuwa suna karb'a. *Kwana tashi* sai gashi an kwashe kwana uku, Hamna dama tare da mahaifinta da tanti Aissata suka zo, sai Amna data addabi Ammar tana so ta zo, da yace ma zai tura mata kud'i su taho tace ita ya barsu tana da kawai zata taho, da ita akayi sadakar uku wacce ta zo da jimamin mutuwar, mutane kuma suna kallonta da magana kan yanda ta k'ara girgijewa ta zama hamshak'iyar mace, haka ma yaranta sun zama yaran gwarawa😂 dumur dumur dasu tubarkallah. *A kwana na hud'u* tunda safe Hassana da Husseina da suka fi kowa jimamin rasa d'an uwansu d'aya daya rage musu suka kira lieutenant, Hassana ce take fad'a masa cewa "Dan Allah Alhaji maganar abincin nan yau dai kawai a canza, idan so samu ne a dafa wake na sadaka, dan ni abun ya fara damuwa wallahi, gidan rasuwa kamar gidan biki, wanda ya zo jiya shine zai dawo yau kuma ba zaka ji yayi addu'a ga mamacin ba, ba jimami babu rakashi da addu'a, shikenan dai shi daya tafi shi ya tafi kawai, ina ganin idan aka rage tukanen da canza abinci kaga wani abu ya sauya." Cikin ladabi lieutenant yace "To Hajka ya za ayi kenan? Har munyi waya da wanda yake kawo mana shanun, yanzu nasan yana daf da kawowa kuma babu dad'i ace ya koma da ita." Husseina ce ta kalleshi tace "To ai ba sai an yanka ba, za'a iya ajewa har wani lokacin." Murmushi yayi ya kalleta yace "Hajia mu zamuyi kiyonta ne? Kawai ku hak'ura na yau kad'ai sai a dakata." Shiru sukayi cikin rashin jin dad'i, fita yayi k'ofar gida sai Zeituna dake jinsu tana wankewa Fatima hannaye ta matso tace "Hajia indai kuna son a dakatar dashi yau to ba Abban Fatima zaku ma magana ba, dan ba zai iya ba shi." Kallonta sukayi Husseina tace "To wa zamu fad'a ma? Shine babba yanzu kuma mai fad'a aji." Dariya tayi tana kallon fuskokinsu tace "Ku ga Ammar, shine zai iya kawai, tsaf zai muku yanda kuke so, amma gaskiya nima abun ya fara hawa min kai na, wallahi idan ana cin abinci wani ya shigo yana addu'a ga mamacin amsawa da Ameen ma wahala yake." Murmushi Husseina tayi tace "Kin ce wani abu kema, tabbas shi zai mana maganin al'amarin, amma akwai buk'atar mu rufe idonmu da kunnuwanmu kan abinda zai fad'a." Daruya Zeituna tayi sai Hassana da tace "Kar mu musa ya ma mutane rashin kunya aje ana fad'armu da sharri." Husseina ce tace "Zai aika, amma kuma Ammar yana aiki da ilimi ai, yana saka komai a muhallinsa ne." Kafin su ce wani abu kam ya shigo gidan d'auke da Abba da yafu rigima sai Imam yana jaye dashi, kallonsu yayi yace "Hajiyoyi barkanku." "Barka Ammar, zo." Cewar Husseina, matsowa yayi yana kallonsu yace "Allah yasa dai ba wasiyya ce zaku bar min ba kuma, dan ba zamu bari ku tafi yanzu ba ku kad'ai kuka rage mana." Dariya sukai sai Hassana da tace "Idan mun tashi tafiya ka rik'e mu to." "To ba laifi." Ya fad'a yana aje Abba, zai fashe da kuka ya sake yin sama dashi yana kallonshi yace "Allah ba dan mai sunanka nan ina k'aunarshi ba da na zabgeka da mari, kaga yaro sai jarabar son jiki kamar mace." Dariya sukayi sai Husseina da tace "Kaga magana zamuyi." Kallonsu yayi d'aya bayan d'aya yace "Wa kuke so a kashe muku?" "Kisa kuma?" Cewar Hassana, Husseina bata damu ba dan ita kayan gidansu ne taji fiye da haka, nan ta fad'a mishi abinda suke buk'ata da tattaunawarsu da mahaifinshi, saida ya gyara tsayuwa yace "Ku fad'i me kuke so ayi to? A watsa kowa ya tafi gidanshi? Ko kuma a musu rashin mutumci mai sanyin gaske da zaisa kowa ya tafi yana jimami? Ko kuma Ko kuma ya kike so." Da mamaki al'amarinshi Hassana tace "Yanzu duk zaka iya yin haka? To tayaya?" Kallonta yayi yana dariya yace "Idan so kike na tashe su ta tashin hankali, barkonon tsohuwa kawai zan sa musu kowa ya watse, ko kuma na musu turaren wuta amma fa na 'ya'yan tattasai, ko kuma na samu mata na biyasu suyi fad'a kamar masu aljanu." Kallonta yayi yana zaro ido yace "Ke Hajia abun fa dayawa da zan iya yi." Da sauri tave "A'a to ba haka muke so ba, kawai muna so muga gidan yayi kama dana mutuwa ne." Kallonta yayi yace "To ku dafa wake, sannan ku samo aduwa da yalo (d'ata) da magarya ku rarraba ma kowa ku ce kayan da Alhaji yafi so ne." Yana yayi hanyar b'angarensu Hassana tace "To ai kar mahaifinka kuma yace ayi girkin." "Ba zai ce ba." Ya fad'a ko juyowa baiyi ba, saida yayi nisa kuma ya dawo da sauri ya tsaya gabansu yace "Wai me yasa ma baku fad'a ma kowa ba sai ni?" Kallon juna sukayi sai kawai yayi dariya yace "Na gane ma, wato ni ne marar mutumci ko?" Sake juyawa yayi yana fad'in "Allah ya shirye ka Ammar." Yanda ya fad'a haka akayi, amma fa babu abinda aka fasa, haka dai aka samu aka kai sati d'aya, a lokacin mutane sun rage sosai wasu ma sun koma garinsu, haka ma mahaifinsu Amna ya koma tare da tanti da ita kanta Hamna, sai Ammar daya shirya tafiya yau shi ma, lieutenant ya nemi daya zauna amma saida ya kalli Ummy yace "Zan zauna Abba idan naga kowa na so." "Kamar ya?" Shine abinda ya tambayeshi, bai ce komai ba sai kallonta da yake, Amna ma kukan shagwab'a ta fara ita ba zata tafi ba wai, saida ya kalleta yace "In ban ci ubanki a gidan nan Amna ki ce d'an iska ne ni, ke ni zaki mayar sakarai, na barki anan ni kuma me zanyi acan ni kad'ai, tunda mukayi aure dake akwai ranar dana tab'a kwana ba'a malamalanki ba?" Ummy da Amna tare suka rufe baki sukayi k'asa da kansu cikin jin kunya, lieutenant kam irin basarwa yayi kamar baiji ba, wata tsohuwa a cikin wanda suka zo daga k'auye na gefe ko gani ba tayi da kyau ta kalleshi tace "Halan Ammaru ne?" Kallonta yayi ya washe baki yace "To dama waye in ba ni ba, Hajja ni ne da kaina?" Cikin takurarriyar muryarta tace "Miye kuma malamalai? Naji kace a bayansu kake kwana?" Ko da Lieutenant yaji haka sai yayi gaba ya fita a gidan dan shi dai yasan halin kayanshi saiya fad'a, Ummy kuma kallon waya aikeki tambaya ta mata, saida ya matso kusan Amna ya janye mayafinta yace "Kin gansu nan." Da sauri Amna ta juya bayanta tana gyara gyalenta, tsohuwar kuma cewa tayi "Ai kasan ba gani nake da kyau ba ko Ammaru." "To bari kiji." Ya fad'a yana sunkuyawa kusanta, saida ya kamo kanta cikin kunne ya rad'a mata "D'uwawu." 😂😂😂😂😂 _In dai tambayar k'wak'waf gareki ai shikenan._ D'agowa yayi ita kuma tasa hannaye ta rufe kunnuwa tana fad'in "Sayadina rasulillahi, Ammaru haka ka zama dama?" Wani kallo ya mata yace "Hajjo daina kira na da Ammaru fa, Ammar zaki ce ko *shugaba*." Cikin fitar da magana d'aya bayan d'aya tace "Shubagan ina kuma? Ni Ammaru na iya to." "Ai ko zan miki fatan mutuwa in kika k'ara kirana hakanan." Tsohuwa najin haka tace "Wai kai baka iya hira mai dad'i bane, to in dai shugaba ne zan fad'a amma bana son hirar mutuwa." Tsuke baki yayi ya k'are mata kallo sama da k'asa ya kalli Amna yace "Kiji fa wai bata son mutuwa, to ko uwar me zata zauna tayi a duniyar, irinsu basa tafiya taya zamu ji dad'in haifo sabbin yaran mu?" Turo baki ta k'ara yi gaba ita dai har yanzu bata son tafiya, had'e fuska yayi yace "Ni kike kumburo ma bakin duniyata?" Sakin bakin tayi tace "A'a." kallon Ummy yayi yace "Mu zamu tafi kuma a yafe mu." Juyawa sukayi inda take biyarsu a baya tana magana da Amna, saida suka kai mota inda Jamil ke jiransu zai kaisu gidan bus ya bud'a yaran suka shiga, zai shiga Ummy tace "Ammar." Tsayawa yayi tare da juyowa yana kallonta, kallon data ma Amna yasa ta zagayawa ta bud'a gidan baya ta shiga ita ma ta zauna, saida ta ga shigarta ta kalleshi cikin taushin murya tace "Ka bar min Ameerah nan, saika fad'a min yaushe zaka dawo?" Kallonta yayi sosai ido cikin ido yace "Ummy Ameera kuma?" Ckkin murmushi tace "Eh, ina son yarinyar sosai kamar yanda nake son..." Kallonshi tayi sai kuma ta sauke idonta k'asa tace "Kamar yanda nake son mahaifinta." Baisan yanda akayi murmushi ya sub'uce masa ba, sosai yake murmushi sai kuma ya turo baki alamar shagwab'a yace "Ummy dama kina so na ne?" Hannu tasa ta mari fuskarshi cikin fad'a tana fad'in "Ubanka Ammar, zan haifeka a cikina ne kuma nace bana sonka? Ina ka tab'a ganin wannan uwar kai? Ubanka ne kai yanzu zaka iya fad'a min adadin son da kake ma yaranka?" Shiru yayi yana kallon sai Ummy data share yar k'wallarta tace "Yaushe zaka dawo yanzu?" Cikin ladabi yace "Zan dawo Ummy ranar da kika ce kina son gani na a gidan nan." Cikin marairaicewa tace "Wai Ammar me yasa kake hakane? Nifa ranar ma magana ce kawai na fad'a maka, amma ba nayi da wata manufa bane." Langab'e kai yayi yace "To Ummy ai ke ce ke yawan fad'in hakanan, saiki dinga hantarata kina cewa na b'ace miki da gani." "To naji na daina ko." Tana fad'a ta juya da sauri ta shige falon, da kallo ya bita sai kuma ya bushe da dariya, shiru yayi alamar yana tunani kafin ya tab'e baki yace "Ina ga fa kunyata ce take ji a matsayina na d'an fari." Kallon k'ofar yayi yace "Zan dawo nan da wata uku Ummy insha Allahu, na miki wannan alk'awarin." Shiga yayi suka d'aga zuciyarshi fal farin ciki na abinda ya faru, yau ma a Niamey suka tsaya kafin su kwana su wuce, tunda suka zo shi dai bai ganta ba ko yaji motsinta, sai dare ya shirya ya fita cikin gari tare da wani abokinshi dake nan, bai wani jima sosai ba ya dawo, tun a farfajiyar gidan ya fahimci anyi bak'o ko kuma bak'i daga yanda yaga wata mota mai kyau a farfajiyar, har zai nufi b'angarensu yaga mutane biyu sun fito daga b'angaren shak'atawa na gidan, kallonsu yale sosai har suka shigo cikin haske, da sauri ya d'ora hannunshi kan k'irjinshi saboda bugawar da yayi, rintse ido yayi yana girgiza kai, saida yaji takonsu na k'aratoshi ya bud'a ido ya kallesu, cije leb'en k'asa yayi cike da bala'in daya fara gurgurarshi, cikin jin masifa a mutu ko ayi rai yace "Hamna ya zakiyi wannan gangancin? Ya zaki jawa bawan Allah firgitar zuci? Me yasa baki tausayina ne? Akan me zaki min wannan d'anyan aikin?" Sake kallonta yayi da kyau, yatsunshi ya fara tank'warawa suna k'ara k'as k'as k'as, to wai uban wa ma ya barta ta fito hakane, wannan ai shi take tona ma asiri, wani shegen d'angalellen wando slim wanda ya bi jikinta matuk'a, bak'i ne wulik baya da kwalliya sai zip d'in dake bakin aljihunshi da suka mishi kwalliyar, rigar ma fara ce fat amma hannayenta sun d'an wuce har gwiwoyinta, daga samanta bud'e yake sai k'asan k'ugun daya matse ya zauna kan k'ugunta d'as, wani kallabi ne kanta irin na kanti fari sol dashi shima, amma kitson atach d'inta ya sauka har gadon baya. A hankali ya fara takowa yana yi kansu har suka game, kallon kallo akuya kallon kura aka shiga yi, kallon.da yake mata babu arzik'i cikinshi, kallon ki fara lissafawa kanki second d'in da suka rage miki a duniya ne, amma kafin nan zan fara kifar da wannan k'aton banzan. Ita kanta gabanta fad'uwa kawai yake, rabon ayi ne da tsautsayi suke bibiyarta yau, dan inba tsautsayi ba bata tab'a yarda ya zo gidan nan ba sai yau daya takurata yana so ya zo ya mata gaisuwa, ta fad'a mishi gidan amma bata d'auka yau zai zo ba sai kawai kiranta yayi yace gashi ya zo, izini ta bayar aka barshi ya shigo ciki, kuma da zuwanshi da yanzun da zai tafi baifi minti goma ba, amma tasan yau sai ta Allah su rabu lafiya, ita abinda ma ke damunta shine babban mutum ne, d'an siyasa ne shima kuma d'an kasuwa, yana da mata da yara uku, bata so ya zubar mata da mutumci kuma shima ua zubar mishi da mutumci, dan shi ba tsoran takife yake yi ba, tana cikin zaro idon nan tana kallonshi taji yace "Malam me ya had'aka da *matata*?" Da k'arfi ta k'ara zaro ido ta kalleshi, shi ma alhajin kallonta yayi da mamaki ya kuma kalleshi yace "Matarka kuma? Ta ina?" Rik'e k'ugu yayi yace "Au! Tambaya ta ma kake? To matata ce ko bata fad'a maka ba?" Hamna ya kalla da mamaki ya ma kasa cewa komai, kallonshi tayi tace "Karka kula shi dan Allah muje na rakaka kawai, baya da lafiya ne." Kallonta yayi yace "Kafin na gama sabautashi ki daure ki min shiru da bakinki, meye na ki na gaggawar son tafiya ke da yau acan zaki kwana." "Ina?" Ta fad'a da k'arfi, saida ya kalli mutumin yace "Lahira mana." Baya taja da sauri tana fad'in "Ammar bana son iskanci wallahi, ka fita a harkata mana." Kallon kumatunta yayi, jinjina kai yayi tare da addua'r Allah ya bashi k'arfin zuciyar da zai uya dalla mata mari, mayar da hankalinshi yayi kan mutumin yace "Bawon Allah kai nake saurare, meya had'aka da matata nace?" Cikin nutsuwa mutumin yace "Kaga, ni ba..." Da sauri ya katseshi da cewa "Ina zuwa, bara ka gani." Wayarshi ya fiddo ya d'an daddana kafin ya nuna masa yace "Idan ba matata bace to ta uban wacece?" K'uri mutumin yayi yana kallon hoton Amna da Ammar suna tare da Ameer Ameera, amma da yake a zaune take kuma ga kama sosai da kwalliya a fuskarta sai kawai ya d'auka tabbas Hamna ce, kallonta yayi yace "Hamna, taya..." Ammar ne ya katseshi da fizge wayarshi yace "Malam saida izini na zakayi magana da ita." Kallon Ammar yayi yace "Kayi hak'uri bawan Allah, ka tabbatar matarka ce ko kuma dai tsohuwar matarka?" Wani kallo ya mishi yace "A ganinka haukana zai iya sa na mallaki wannan kayan kuma na rabu da ita? Kai ba kayan bane ka biyo?" Matse baki kawai yayi yace "In kuwa har matarka ce yanzu to akwai buk'atar ka sake saka ido akanta, kayi hak'uri." Kallonta yayi yace "To kai baka ganta bane? Mahaukaciya ce fa ta sakawa a gidan gaba, yanzu haka magani take d'auka." Girgiza kai kawai mutumin yayi ya wuce abinshi, kallonshi tayi sai kawai ta fashe da kuka ta juyawa da sauri zata koma ciki, da k'arfi yasa hannu ya jawo gashinta yayo baya da ita, sam bata tsammanin haka ba sai kawai ta fad'o a jikinshi gaba d'aya, cit wurin yayi kafin ta fara k'ok'arin tashi da k'afarta, sakinta yayi ta mik'e daga jikinshi inda suka sake kallon juna, cikin masifa da neman sababi tace "Wallahi Ammar ka fita a hanyata, ya zaka korar min saurayi na wanda nake tunanin shi zan aura? Kana da matsala dani ne?" Sunkuyar da kansa yayi ya d'ago idonshi kamar wani zaki yana kallonta, tambaya yake wa kansa me yasa bata nesanta kanta da wasu ne? Ya jima yana kallonta haka ita ma tana kallonshi kafin ya gyara tsayuwa yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _58_ "Hamna ame kika d'aukeni?" Sauda ta d'aga masa gira sama ta kalleshi tsaf sannan tace "A babban mah...mana." Wani kallo ya mata jin rainin hankalin data masa, mahaukaci take so tace amma shine bata k'arasa ba, kenan mahaukaci take kallonshi? Ai kuwa zai nuna mata a aikace, matsawa yayi kusanta zaiyi magana sai ta k'ara ja baya tace "Malam tsaya daga can mana." Jiniyar motocin da suka ji ne yasa su juyawa duka suka kalli k'ofar, mahaifinta ne ya dawo cikin rakiyar masu bashi tsaro kamar kullum, suna kallo akayi pakin motocin aka bud'e mishi ya fito, sauran motocin duk wajen ajiyesu aka nufa dasu inda wasu jami'ai biyu ke biye a bayanshi, kallonshi tayi ta harareshi sama da k'asa ta juya baki tare da jan dogon tsaki tace "Malam ka shirya saina sa ka bawa saurayi na hak'uri, sannan da kanka zaka bashi aure na a matsayinka na babban yayana." Shigewa tayi a lokacin kuma mahaifinta ya k'araso, saida ya d'an rumguma Ammar a jikinshi suka gaisa, tare suka shiga babban falon, suna shiga Aissata ta tarbe shi sai ma'aikata da suke ci gaba da gyara wajen cin abinci, Ammar kuma kallon kawun nashi yayi yace "Ina zuwa tonton." Bayan Hamna ya bi data haye sama d'akinta, ko zaune ba tayi ba taga ya fad'o mata d'aki yana cire mata cazar waya a jikin bango data saka, da mamaki tace "Malam lafiya? Me ya shigo da kai d'akina?" Rintse ido yayi ya sake bud'esu akan ta tarau, da k'arfi ya d'aga cazar ya zuba mata a baya, wata uwar ihu ta sake tare da juyawa ta fara taka rawar da babu shiri tana matse k'afafunta da taji fitsari na barazanar danno mata kai, kuka take da iya k'arfinta ta rasa me ke mata dad'i, bata gama jin azabar ba taji ya shak'o wuyan gashinta a daidai infa ta d'aureshi da ribom ya jawota, hannu tasa ta rik'e hannun nashi d'aya kuma ta rik'e rigarshi daidai mab'allan rigarshi tana sakin wani kukan tana fad'in "Kayi hak'uri yah Ammar, kayi hak'uri dan Allah ba zan sake ba, karka dake ni dan Allah na tuba." Tunda suka ji ihunta suka d'aga kai sama suna kallo, suna ganinsu ya sauko da ita k'asa har gabansu ya gurfanar da ita, tonton ya kalla fuskarshi babu alamar ya tab'a dariya a rayuuwarshi yace "Ku zama shaidata, wallahi saina karya yarinyar nan idan ta sake tara mana yan iska a gida, sannan..." Ya fad'a yana sake kallonta yace "Ki tattara kayanki gobe zaki koma gida, nan dan kinga babu mai saka miki ido yasa kike abinda kika ga dama, to zaki koma can gaban Hajia da Ummy." Cazar hannunshi ya jefa mata a jiki ya sunkuya ya nuna ta kamar zai tsone mata ido yace "Ki tuna da cewa indai akwai rai da rabo, sannan akwai lokaci to wata rana zanyi iko akan ki." Kamar zai taka ta haka ya wuce ko kallonsu tonton bai sake yi ba, da kallo ya bishi baki sake, shi fa ba mamakin abinda yayi bane yake bashi, kalamanshi na k'arshe da kuma yanda abun ya b'ata mishi rai, to duk me yayi zafi haka? Dawo da kallonshi yayi kanta yace "Koma ciki, sannan ki had'a kayanki gobe zaki koma, ba zan iya jarabar yaron nan ba." Cikin kuka ta mik'e tace "Wallahi Abba babu inda zanje, haka kawai sai kace wani uba na." Nunata yayi da yatsa yace "Ke ki bar bala'i yayi kwana, ina ce yanzu a gaban uban naki ya miki wannan k'wak'waran kashedin? To dan haka ki d'auka ma yafi ubanki." Tumurmusa k'afafu ta shiga yi tana fad'in "Allah Abba ba zan koma ba, ni nafi son zama anan, kawai dan ya fad'a shikena ba zaka ce masa komai ba." Matsawa yayi kusanta ya dafa kafad'arta cikin taushin murya yace "Yar albarka, kiyi hak'uri ki tafi kinji, shi da gobe ne zasu tafiyarsu, daya tafi saiki dawo idan haka kike so, pour les moment dai ki tafi kinji ko." Jinjina kai tayi tace "Ok Abba, amma ka fad'a masa ya daina takura min ya fita a harkata, inba haka ba zan masa rashin mutumci." Jinjina kai sha yayi ya shafa kanta yana kallo harta haye sama, kallon Aissata yayi wacce ita hausar ma bata gama ji da kyau ba yayi murmushi, ciki ya wuce da jinjina al'amarin yaron nashi mai kama da d'an uwanshi colonel a zafi. Saida ta gama shiri tsaf yace ai tafiyarsu ba yau ba saiya koma gida, bata nuna bata ji dad'i ba saboda gudun tashin k'wank'wamanshi dan su rabu lafiya, da addu'a ta rakashi sam bata san tare da wa zai tafi ba, har d'akinta yaje ya tisota gaba suka fito, a motarshi daya bari suka d'auki hanya inda Hamna take addua'r sauka lafiya, gudu yake na ganganci da kauce k'a'ida, ita har ga Allah tasan a d'ane yake jaraba yake neman, a yanda yake tasan ko jami'an kan hanya yau saita Allah su rabu lafiya, ita kuma ba zata so ya ja mata kwana a magark'ama ba, a hankali ta kalleshi cikin rawar murya tace "Yah Ammar ka tafi a hankali dan Allah, kana taka doka fa." Ashar d'in daya malmalawa masu dokar da wanda ma aka d'orata yana wajen yasa ta ja baki tayi shiru tana girgiza kai, shirun da tayi kuma wata masifar ce sai ya fara fad'a wai ta maida shi mahaukaci tayi banza dashi, cikin salon rashin kunya tace "To Allah ya huci zuciyarka, bana so nayi laifi ne." Damtsen hannunta mai tarin tsoka ya mara yana fad'in "Ba dan kin raina mutane ba, wai ke har ki fito da wandon daya kamata ace mijinki ne kawai zai gani a gaban namiji, to me kile son nuna masa kenan? Ya gani yayi sha'awa ko me?" Ta wutsiyar ido kawai tale kallonshi ba zata yarda tayi magana ba ya sata a boot ya rufe, cikin masifa ya sake cewa "Ke ko can na kaiki kika k'ara kula wani Hamna saina babbaka d'an iska sai dai uwarsa ta haifi wani." Baki bud'e ta kalleshi tace "Saboda me? Akan wane dalili? Kar nayi aure kenan kake nufi?" Shiru ya mata baice komai ba dan haka tace "So kake na zauna haka har k'arshen rayuwata?" Ba tare daya kalleta ba yace "Zakiyi amma ba yanzu ba, zan samo miki wanda ya dace." A ranta tace "Bigagge kamar ko?" A zahiri kuma tab'e baki tayi ta kalli titi, suna cikin gudu sosai wata mota ta giftasu da gudu tana zabga oda ita ma ta wuce, zuro kai yayi tsabar neman fitina yace "Idan kunje ku d'auke hanyar kusa aljihu kar mu wuce." Dawo da kanshi yayi yana fad'in "Yan iska kawai mashaya." Ajiyar zuciya ta sauke ta rumgume hannaye, kallonta yayi ya taka birki da k'arfi yace "Meye? Na dameki? To koma baya." Zage ceinture d'inta tayi ta bud'a zata fita dan tafi son haka ma sai kuma ya jawota da k'arfi ya zaunar da ita yace "Ba zaki koma d'in ba tunda ba drebanki bane ni, kenan ma da gaske na dameki ko? Ba komai Hamna Allah yana gani." Gyara zamanta tayi ita dai ba tace komai ba har ya sake d'aukar hanya, kallonshi tayi kallo na nutsuwa da basira, yayi shiru abinshi, shigar yan gayu ce jikinshi bleue d'in jeans da bak'ar riga mai dogayen hannu amma ya lank'washe su har zuwa gwiwar hannunshi, takalminshi k'afa ciki bak'i masu kyau, gemun nan yayi luf dashi sai walk'iya yale idan suka gifta ta cikin rana, zara zaran gashin idonshi wanda ke rufe girman idonshi duk sanda ya rufe su, kakkaurar girar mai yalwargashi da tsayi, dogon hancinshi daya tafi daidai da tsayin fuskarsa abun gwanin sha'awa, amma kuma kyawun d'an maciji ne, nan idan yayi wani abun saika rantse a gidan mahaukata ne yake. D'an kawar da kanta tayi ta kuma kallonshi har yanzu dai hankalinshi na ga tuk'i, cikin sanyayyan murya tace "Kai likitan zuciya ne, amma me yasa baka tsoron saka mutane a damuwa?" Saida ya fara d'aga idonshi sama sannan ya d'an kalleta, da alama nutsuwa ta zo mishi dan cikin sanyin murya shima yace "Ba damuwa nake saka mutane ba, ina musu magani ne." A hankali tace "Comment?" Kallonta yayi sosai sai kawai yayi murmushi mai sauti yace "Tu ne comprends rien, rien Hamna." Kallonshi tayi tace "Me yasa kace haka?" Ba tare faya kalleta ba yace "Peut être wata rana." Cikin odonshi ta kalla tace "Ammar je te connais bien, (na sanka sosai), mai jusqu'à présent je ne comprends rien (amma har yanzu bana fahimtar komai a game da kai)." Dariya yayi wacce ta fito da hak'oranshi yana girgiza kai yace "Idiote." Kallonta yayi yace "Dana bari kin fahimce ni da kin k'ara tagayyara ni kankana." Da mamaki ta kalleshi tace "Kamar ya?" "Comme je le dit (kamar yanda na fad'a)." Ya fad'a yana kashe mata ido d'aya, girarta ta d'aga sama ta kalli titi tace "Moi aussi." Kallonta yayi yace "Ke ma me?" kallonshi tayi tace "Dana tagayyari daka gane." Bushewa yayi da dariya yace "Ni na sani dama." Da sauri ta kalleshi tace "Vraiment?" Sake kanne maya ido yayi yace "T'inquiète pas ma puce, chaque chose a son temps, petit à petit les oiseaux..." Sai kuma ya bushe da wata dariyar yana k'yalk'yalewa da ita, ita ma da bata fahimce shi ba sai kawai taji ta bushe da dariya, kallonshi take tana tayashi dariyar kamar zararru, sun jima suna dariyarsu kafin suka tsagaita kuma akayi shiru, kallonta yayi yace "Me kika ma dariya?" "Abinda kake ma." Ta fad'a tana hararenshi, da wannan ne sai tafiyar tasu ta d'anyi dad'i, dan har tsayawa yayi a station d'in Alhaji suka sha mai suka wuce, haka ma saida ya siya mata kayan k'walama suka ci, tafiya tayi nisa sosai kawai ya tsayar da mota a gefe ya kalleta yace "Fita kiyi fitsari yarinya karki min shi a mota." Da zata ce masa bata ji, sai kuma taga ya raina mata hankali ma sai kawai tayi banza dashi, cike da zolaya yace "Ko na siya miki 4 (kun dai gane kalmar da english ai) ne kiyi?" Fuska a had'e ta kalleshi tace "Eh, ko kuma penpers ba." Wani kallon shak'iyanci ya mata yace "Wannan ki bari sai zaki fara bulbuli." Yamutsa fuska tayi tace "Bulbuli kuma? Yara fa ke bulbuli." Kallon baki da hankali ya mata yace "Waccen bulbulin nake nufi wanda ku kukeyi duk wata." Murmushin baka da hankali ita ma ta masa tace "Da har na fara tunanin ko an canza ka ne da naji baka saka kaina yayi nauyi ba, amma yanzu na ji na gamsu da kai nake tare." Wayarshi ya d'auka yana dannawa inda Hamna ta gyara zamanta ta jingina sosai, Amna ya kira suka gaisa tare da shiga hirarsu ta soyayya, tana kallonshi har bacci ya d'auketa a haka, yana idawa ya kalleta, murmushi kawai ya saki ya ci gaba da tuk'i cikin aminci. Ganinsu tare ya ba kowa mamaki, har d'akin Hajia ya kaita ya gindaya sharud'anshi wai ko fita karta sake yi ba tare da dalili ba, saida ya gama tsaf Hajia ita dai ta kalleshi tace "To za'a kiyaye." Ummy kuma kallon al'ajabi take da ikonshi, inda Hassana da wasu daga cikin dangin Hajia suka bishi da kallo suma, har zai fita Hamna ta fara gunguni k'asa k'asa tana fad'in "Wallahi babu wanda ya isa ya hana ni fita tunda ba yar zaman banza bace ni, kaji mutum kamar wani uba na ehee." Juyowa yayi ya kalleta yace "Ki jaraba ki gani to." Fita yayi duk suka raka shi da ido, a ranar dai kamar wasa Hamna ta rantse cewa ba zai hanata abinda tayi niyya ba kamar wanda ya haifeta, kai ita ko dan ta nuna mishi bai isa ba ma saita fita a yanda ta ga dama d'in. *Washe gari* tsaf ta shirya dan zuwa salon d'inta, doguwar riga ce ta saka ta kanti kuma ta mata kyau sosai, kallabin rigar ta yane kanta dashi ta fito, a falon suka had'e yana sallama da su Hajia zai wuce, gaisu tayi tasa kai zata fita tsohuwa mai tambaya😂 tace "Amina (yanda take kiransu kenan) banji kin gaishe da shugaba ba?" Juyowa tayi ta kalleshi sama da k'asa tace "Tsohuwa wane shugaba kuma?" "Ammaru mana, ba yayanki bane da zaki fice baki gaishe shi ba?" Cewar tsohuwar, tab'e baki tayi tace "Sauri nake Hajjo." Cikin rarumar gani tace "Ina Sa'ada take?" Ummy dake rik'e da kular abinci ce ta tsaya tace "Hajjo gani, wani abu kike so?" Cikin dattako tsohuwar tace "Yanzu Sa'ada kina ji Amina bata gaishe da yayanta ba kuma baki mata magana ba?" Kallon Hamna tayi da ita ma take kallonta, rasa abin fad'a tayi sai Ammar daya kalleta yace "Ki rik'e gaisuwarki ma, kije ki saka hijab kawai saman jayan nan naki." Cike da raini tace "Doguwar riga ba'a saka mata hijab, ko baka san haka bane?" D'auke kanshi yayi daga kanta yace "Ki canza wasu kayan da zaki iya saka hijab." Cike da gatsali tace "Malam wai me ya maka zafi ne da shigata? Ina ce haka kuke son gani?" Hajia ya kalla yace "Hajia dan Allah ban son tashin hankali, ki fad'a mata ta dinga rufe jikinta kafin ta fita, nan fa babban gida ne da ake ganin mutumcinmu, ita kad'ai bai kamata ta zubar mana da daraja ba, ni ina ga ko dan rasuwar da akayi zata iya kama kanta ai." Dariya tayi tace "Kama kai? To wane irin kama kai kuma bayan ko ka kama shi akwai masu warware maka, kaga malam ka fita a hanyata idan kana da zuciya dan Allah, kuma fita haka zan fita na ga wanda zai hana ni, zaka zauna kawai kana sa min doka kamar kai ka haifeni, bayan kuma duk wani mugun abun kaine ka fara shi, saika nuna kai na Allah ne amma kuma ba haka bane, to idan tayar maka da hankali nake ka fad'a min inda zamu had'u, a shirye nake yanzu tunda na ga abinda kake so na zama kenan." Saida ta dasa aya, ta kai k'arshen abinda take son fad'a, d'ago kai yayi ya kalleta ido cikin ido, idonshi sun canza kala sunyi ja, maganarta ta sokeshi fiye da tunanin mai tunani, ta kassara zuciyarshi da kalamanta, ta sa shi jin kunyar soyayyar da yake mata, zai kuma nuna mata a aikace ba yanda take tunani yake ba. A sukwane ya mik'e yayi kanta, saida ya tsaya gabanta ya d'aga hannunshi mai d'auke da zarta zartan yatsu ya sauke mata kyakyawan mari a fuskarta, kafin ta d'ago daga sunkuyawar da tayi tare da k'ara ya sake sauke mata wasu yatsun, ta dafe kunci zata d'ago a karo na uku ya sake gabza mata wani marin, rud'ewa tayi ta ja baki tayi shiru daga ihun da take tana murza kumatu da taji suna mata wani zuuuu zuuuu zuuuu kamar zasu tsinke, daga wayarta jaka da makullin mota duk ta jefar dasu, sam babu abinda take ji sai ko take gani, tana cikin wannan halin ya sunkuya ya nunatada hannu yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _59_ Cikin matsanancin b'acin rai yace "Hamna ni? Ni zaki kalla ki fad'a ma wannan maganar? Yaushe aka haifeki? Yaushe har na miki caccakar da kike ganin ta isa ta zama katangar da zaki b'uya a bayanta ki raina ni? Ko yar uwarki da nake kwana tare da ita na tashi tare da ita babu kaya a jikina bata isa ta min rainin da kike son min ba, har ki kalle ni wai kice na fad'a miki ina zamu had'u, ke yanzu nan har kin shirya zaki iya dani? To saurara kiji Hamna ba tsananin so ko kishinki bane yasa nake takuraki kan dinga suturta jikinki, mutumci ne nake so na kankaro miki a idon jama'a, duk idon mutane yana kanki saboda daga babban gida kika fito kuma yar babban mutum ce, amma daga son taimaka miki sai abu ya zama tashin hankali." Kujerar daya tashi daga kai yasa k'afa ya tokara cikin b'acin rai kujerar tayi baya da k'arfi ta daki kwabar gilas d'in turare, hakan yasa wasu daga cikin kwalaben girgizawa suka fad'o k'asa hakan ya haddasa sauti marar dad'i mai kayar da gaba, bai kula ba yasa hannu yana dukan k'irjinshi yana fad'in "Allah ma shida ne, sannan kuma ku zama shaida." Ya fad'a yana nuna duk mutanen dake d'akin yace "Inhar na k'ara magana kan Hamna ta suturta jikinta ku ce ta hanyar zina aka haife, na kuma yarda ba zanyi gadon mahaifina ba, ba wai iya dukiyarshi ko d'aukakar shi kawai ba, har da sunan shi, na yarda ba zan sake saka sunanshi a gaban suna na ba." Kallonta yayi yace "Kiyi duk abinda kike so da rayuwarki, banda matsala a kai Hamna." Da saurin bala'i ya fita daga falon zuwa barin gidan gaba d'aya, yana tuk'i yana dukan sitiyari da k'arfi. Falo yayi shiru ko numfashin mutane baka ji, wasu tunda suka rintse ido sakamakon fad'owar kwalaban turare basu bud'e ba har yanzu, Ummy da hankalinta ya gama tashi tasan yau asirinsu zai tonu, dan dukansu sunyi magana ne a yaran da duk mai hankali zai fahimta, kallon Hajia take da taga kanta k'asa tayi shiru, a hankali ta juya kanta ta kalli Hajjo, sai taji tsohuwar ta bata haushi dan duk ita ta b'abb'ako musu aikin nan, data barta ta tafiyarta da yanzu an rabu lafiya. Kakkauran numfashi Hajjo ta sauke cikin muryar alhini tace "Hajia, dama haka yaron nan yake?" Hajia ma da tasan komai kuma bata so abun ya fito kallonta tayi cikin jin haushi tace "Duk ke kika ja mana wanan sababin fa, da bakiyi maganar gaisuwar nan ba duk da haka bata faru ba." Kallon Hamna tayi da sai yanzu kad'ai take jin magana a hankali a hankali tace "Ki tashi daga nan ki bani wuri, kije kiyi ta fita duk yanda kike so babu mai hana ki, idan kina so ma ki tafi tsirara, amma karki kuskura ki zubar mana da mutumcin gida kinji na fad'a miki." Tana fad'a ta mik'e tayi d'akinta, Ummy na ganin haka wata ajiyar zuciya ta sauke tana godiya ga Allah, ita ma sulalewa tayi ta bar wurin ko Hamna bata kula ba dan maganar gaskiya tasan Hamna ce ta jawo magana, shi kuma dama ba hak'uri gare shi ko na k'wayar zarra. Hamna ma mik'ewa tayi cikin hassala ta d'auki jaka wayarta da makulli ta fita, ko da ta shiga mota saida ta gyara fuskarta da duk sawun hannayensa suka fito, wannan haushin na cin zarafin daya mata da kuma abinda Hajia ta fad'a mata yasa ta niyyar ba zata canza d'in ba, haka ita ma ta fita daga gidan rai a b'ace, ko da taje salon saida tasa aka nemo mata maganin ciwon kai tasha dan gaskiya fa tasan ta maru, mari ne data tabbata daya sake mata na hud'u to kunnenta ko idonta zasu iya barin k'wallon kanta. Mutanen wurin babu wanda bai fahimci me ake nufi ba, anyi shiru ne kawai saboda babu wanda ya isa yayi magana, sai dai kowa ya yarda Hajia ma tayi shiru ne yanzu saboda abin daga iyalinta ya fito, amma da wasu ne da tuni ta cire musu wando ta kai ta bisu da dariya, sannu sannu maganar ta fita daga falon ta kai farfajiyar gida, daga farfajiyar gida ta fita k'ofar gida, to fa iska na surarta yayi gaba da ita har wasu garin ma saida aka ji wannan tsirku, inda aka ma maganar ado da kwalliya cewa Hamna yar iska ce kawai, shiyasa ba tayi aure ba kuma ana gani an saka mata ido, iskancin ne ma ke tsakaninta da mijin yer uwarta, nan fa kowa ke fad'in albarkacin bakinshi, inda wasu ke fad'in ai muna ganinta cikin garin, tun tana hawan moto dama take more rayuwarta, yanzu kuma da take hawa mota ko magana ba ayi ba, wasu kuma fad'i suke ai sun ganta biki kaza da kaza ko kuma wacce da wacce ce k'awayenta, mutum kenan mugun icce. Haka akayi rabon gadon Alhaji inda kowa yaja nashi babban rabo😂, kowa ya k'ara yawan jari ya kud'ence abinshi, shagali kawai ake iyaye da yaransu, kowa ya k'ara d'ora yaranshi kan manyan harkoki, hakan ya tilastawa Ammar dawowa wata ukun bai cika ba aka duk'ufa harkokin duniya, wani lokacin kamar kanshi zaiyi bindiga tsabar abunuwa, yaje asibiti yaje station shaguna da sauransu, a hakan ma wai dan Amar ma da inda yake kulawa haka ma Kamal suna saka shi kowane b'angare tunda ya fara mallakar hankalinshi shi ma. Tunda abun nan ya faru ko sannu shi da ita bata sake had'asu ba, ya watsar da al'amuranta ya sake rumgumar matarsa hannu bibbiyu, sau da dama sukan had'u ko wajen shiga mota ko farfajiya ko k'ofar gida ko kuma falon Hajia, amma kallonta ma baya yi bare yaga shigar jikinta abun ya dame shi, hasalima ko ganinta yayi canza fuska yake yi yayi abinda ya kawoshi yayi gaba. *Wannan* shi ake kira da kisan mummuk'e, gashi dai ya fita harkarta kamar yanda take fad'a a kullum, ya daina ko kallon fuskarta, ko d'akin matarshi zai shiga ya ji tana ciki saida ya koma har sai ta fita, tun tana jin kamar dad'i take ji har ta fahimci ba dad'i take ji ba a zuciyarta, kawai tana nuna tana jin dad'in ne a zahiri, ita ma bata kula shi kamar yanda yake yi, sai dai bata jin dad'i ko kad'an. Amma kuma hakan baisa ta canza abinda duk shine ya jawo matsalar ba, sabon babin rashin mutumci da fitsara ta bud'e, Amie dama ita ma ba aure tayi ba dan haka ta taya b'era b'ari suke sharholiyarsu, yawan biki da bi-gari kullum cikinshi suke, sun shiga sahun manyan matan da ake kiran sunansu, wannan matsatsun kayan dai kullum sune jikinta, wani lokacin ko gyale bata d'orawa haka zata shiga mota. Kud'i kullum cikin kashesu take wajen siyan anko na k'awaye da d'inki, anko ba wai guda d'aya ba a'a sama da haka, abune daya zama na yayi kowa na so a fad'i bikinshi, hakan yasa kamu bridel party kan amarya damu, duk wannan abubuwan anko ake fiddowa kuma tana siya da kud'i, wasu lokutan d'inkin da akayi iri d'aya akeyi duka yan mata, wani d'inkin ko wata shigar idan kaga sunyita ka rantse ba yayan musulmi bane. Amar ne ma ya d'an fara k'orafi kan abinda take, shima daga baya ya ja bakinshi yayi shiru, Hajia na gani amma an rasa dalilinta na saka mata ido tana abinda ta ga dama, Ummy ce ke tsaye kanta take mata fad'a da magana, amma magana d'aya ce "Ummy ki yarda dani wallahi ba zan tab'a zubar muku da mutumci ba, ko ban fita biki ba ai zan je wajen sana'ata, dan haka ki kauda idonki daga abinda mutane zasu ce ko suke fad'a." Hadiza taga canji sosai a game da yar ta ta, hakan yasa ta tambayi yar uwarta Amna, a lokacin Amna ta ji a cikin gidan cewa Hamna ta ma Ammar rashin kunya shi kuma yace ba zai k'ara mata magana ba, yanda taji ta fad'a ma uwar wanda hakan yasa ranta b'aci fiye da kima, a waya ta kirata ta fad'a mata tana son ganinta, wannan karan ko da ta zo ko wurin zama ba'a bata ba bare ruwa aka balbaleta da masifa, ta inda Hadiza ta fita bata nan take fita ba, ta mata fad'a sosai kamar yawun bakinta zasu k'afe, tana gamawa kuma tace ta tashi ta koma bayan ta bata umarnin ta fito da miji wata d'aya kawai idan ba haka ba kuma zata dawo da ita gabanta ko da hakan zaisa sai tayi shari'a da dangin uban nata, haka ta juyo ta dawo tun a hanya take tunanin abinda mahaifiyarta ta fad'a, cikin jin haushi take tambayar kanta waya fad'a mata abinda ya faru? Wa zata fitar a matsayin miji? Ita fa bata shirya aure yanzu ba ma, idan fa tayi auren ma asiri ya tonu fa?Tsaki tayi ta d'an daki sitiyari saboda tuna abinda mama ta fad'a, a hankali ta shiga jero kalmomin data fad'a mata a k'walwarta. *"Ashe shiyasa kika zama tsagera, saboda mai fad'a aji a gidan ya tsame hannayensa daga kanki, to ke inba hauka irin naki ba duk gidan nan waye zai tsawatar miki inba Ammar ba? Sa'ada dama ba mazauniya gida bace, sannan tun farko ita da lieutenant sun riga da sun lalata ku da sangarta, colonel a shekara d'aya zaman da yake a gidan lissafaffe ne, Labaran kuma dama tun farko baya shiga sabgar iyalin Hajia saboda baya son ta ci zarafin mahaifiyarshi, dan shi zai iya yin laifi amma har Hajiarshi saita wanke ta tas, to Amar Junaid Jibril dukansu aikin banza ne, babu wanda ya damu dake ko tsirara zaki fita, mahaifinku kuma kinfi kowa sanin baya da lokacinku, to ki fad'a min inba Ammar ba waye zai sa ido akan ki? Ke ba ma ke kad'ai ba kaf yaran gidan shi kad'ai ne mai taka musu birki, dan haka ki same shi ki bashi hak'uri in ba so kike kiga b'acin rai na ba."* Shawarar Amie tayi aiki da ita wajen fito da *Habib* a matsayin wanda zata aura, ba wai dan tana son shi bane sai dan shine yafi tsarin da take son mijin aurenta ya kasance, ba'a wani tsaya bata lokaci ba aka shigar da manya maganar kuma suma suka nuna manyantaka, dan danan aka saka rana inda aka kawo kaya, k'ok'arinshi ya birgeta dan yayi bajinta sosai. Matashi ne dake da jini a jika da ji da dala, nan fa, matarshi d'aya da yara biyu, nan aka fara shirye shiryen bikin Hamna su Amie aka fara shiga da fita, sai lokacin take tambayar Hamna me ke tsakaninsu da Ammar? Saboda taga sun had'u shi zai fita su zasu shigo ko kallonsu baiyi ba, data fad'a mata abinda ya faru sai ita kanta taji ta samu damar da zatayi aure, dan dole ta shigar da kanta wajenshi, ta mayar da wasa gaskiya ta zama mallakinshi, fad'ansu da Hamna kuma nasara ce wurinta, dan hakan na nuna Hamna ba zata shiga abinda ya shafeki ba, ma'ana ba zaisan komai a kanta ba, tunda k'awayence ne ake abisa taka dokar mutumtaka, Hamna tasan Amie sarai tasan rikakkiyar karuwar alhazan birni ce, amma duk da haka tana tare da ita, wanda hakan ma ya taka rawa sosai wajen goga mata pantin da ake mata kallon mutuniyar banza ita kanta. An fito da anko kala har hud'u, sun shirya sun had'u da abokan ango sun fad'a musu abubuwan buk'atarsu, sun d'auki wanda hankali zai d'auka sun aje musu sauran, shirye shirye sunyi nisa sosai, amma har yanzu Hamna bata jin farin cikin da wannan aure, tana yin komai babu kuzari a ciki ko alamar so, idan suna hira da Habib wani lokacin Ammar ya kan shigo gidan, a matsayinsa na musulmi kuma wanda ya ga mutane yana sallama ya kuma bawa Habib hannu su gaisa, amma bai tab'a yarda idonshi da nata sun had'u ba sai dai ya fice, haka zata bishi da kallo har ya b'ace ma ganinta, haka ita dai take sukuku sai lokaci kuma dake k'aratowa. *Har* bacci ya fara gaba dashi Amna ta tashe shi kan ya manta bai siyo madaran daya yara sabonta ba, kowa zai iya bacci bai sha ba amma banda *Ameera*, saida ya lumshe ido yace "Ke dai kina jin bak'in cikin kiga na kwanta baccin alhalin ke ma baki kwanta ba ko?" Dariya tayi tace "Ta ya ba zan so ganinka kana hutawa ba? Ai farin ciki na ne." K'ok'arin saukowa daga kan gadon yayi yana fad'in "K'arya kike, ai da sai ki tuna min tun kafin na shigo gidan." A hankali tace "Wallahi na manta ne gaba d'aya, kuma naga tun kafin ta ida kake kawo wata." Cikin sumalin bacci yace "Bansan ya akayi bane na manta wallahi, yanzu kuma zata hana kowa bacci a gidan nan in babu ita." Da kallo ta bishi har ya canza kaya zuwa k'anana ya d'auki makulli yana fad'in "Allah yasa a samu a kusa." Suna fitowa a falo ta samu Ameera kwance yanda ta barta tana ta latsa remonte tana canza tasha, kusanta ya matsa ya sunkuya yace "Gimbiya Ameera, yarinyar mamanta da babanta, yarinya yar baiwa mai sa'a, shalelen Ummy da Abba, zaki sha bonbon (alawa)?" Kai ta girgiza mishi tare da cunno baki gaba cikin muryarta ta yara tace "A'a ni madaya na ke co." D'agowa yayi ya kalli Amna yace "Duk yanda akayi ke kika sa mata akai ta daina yarda duk wayon da za'a mata." Dariya tayi tace "Banda abun uban yan biyu waye zai shiga tsakaninka da yaranka?" Ameera ya kalla yace "Muje to ki raka ni na siyo ko." Tsil ta diro daga kujerar tana jujjuyawa inda zata ga takalminta, tana ganinsu ta d'auka tasa ta rik'e hannunshi, saida ta juyo ta ma Amna bye bye tace "Ummy sai mun dawo." "A dawo lafiya." Ta fad'a tana zama, kallonta yayi yace "Me kike so na taho miki dashi?" D'an d'aga ido tayi alamar zatayi tunani yace "Zaki sha ayaba?" Kallonshi tayi saita yamutsa fuska tace "Bana jin dad'inta yanzu." Tsayawa yayi yana mata wani shu'umin kallo yace "Tunda kika samu tawa ko?" Bushewa tayi da dariya tare da rufe fuskarta da hannu d'aya tana fad'in "Ba haka bane." Hararanta yayi yace "Ba haka bane kamar ya? Kin samu lafiyayya kina ta moreta tana zazzaga miki yara bigu biyu biyu dole ki ce wannan ta fita a ranki, to kiji da kyau ita wannan d'in da kika raina sanfirin aubangiji ce." Tsayar da dariyarta tayi tace "To ai ita ma waccen d'in hakane." Juyawa yayi yana fad'in "Tunda kince haka bari na dawo yau zan sake baki ajiyar wasu yaran, amma wannan karan uku zan ajiye." Murmushi kawai tayi ta bisu da kallo, wannan magana kamar ya fad'a ne daidai amsawar mala'ikun rahama, a ranar ta gama al'adarta ta kimtsa kanta dan farin cikin mijinta, dama magani ne Ummy ke d'orata akai wanda shi tafi so, a ranar ma tasha zuciyarta babu tunanin komai, amma da yake akwai tsananin rabo sai gashi duk da babu tabbacin a wannan dare ya shiga amma daga lissafi za'a gane a wannan lokacin ne. Sanda ta fara jin alamu ta d'auka ucler d'inta ce kawai ta zo mata da sabon salo, amma sai abun ya fara damunta ganin tana shan maganinta kuma a banza, saida taji bata son warin gas d'in da take aiki dashi ta fara tunanin ciki ne da ita, da sauri ta d'auki tsinken gwaji ta ma kanta, ai kuwa dai ta tabbata abinda take tunani, zaune tayi kan gado jiki a sanyaye ta dafe kai da hannaye biyu, k'walla taji sun cika mata ido tana shirin yin kuka, shigowarshi tasa ta zabura tana goge hawayen, b'oye tsinken tayi a hannunta tana kallonshi, shi ma wani tuhumammen kallo yake mata har ya tsaya gabanta yace "Lafiya?" Kai ta girgiza masa kawai tana shirin fita daga d'akin, rik'ota yayi yana kallon fuskarta yace "Fad'a min me ya faru?" Fuskarshi ta kalla sai kawai ta fashe da kuka ta fad'a jikinshi, cikin tashin hankali yace "Ke Amna lafiya? Me ya faru ne wai? Me aka miki? Ni ne na tab'a ki?" Share hawayen ta fara yi hakan yasa shi tallabo fuskarta yana fad'in "Kiyi hak'uri idan nine na b'ata miki rai kinji, ban sani ba wallahi." Girgiza kai tayi alamar a'a, had'e girar sama da k'asa yayi yace "To me ye kike ma kuka?" A hankali ta nuna masa hannunta ta bud'eshi daga dunk'ulewar data masa, hannu yasa ya d'auki tsinken ya duba sai kawai ya kalleta yana murmushi yace "Kice min har na cika aiki?" Cike da damuwa tace "Yah Ammar bana so? Ciki ne fa?" Da mamaki yace "Ba kya so Amna? Cikin na wa?" Marairaicewa tayi tace "Yah Ammar ka fahimta mana, duka fa aurenmu har yanzu bamuyi shekara hud'u ba." Ba alamar wasa yace "Sai akayi me?" Turo baki tayi tana d'an juyawa tana fad'in "Ni gaskiya bana so, haba kamar wata kaza." A hankali ya juyo da ita gabanshi yana kallon idonta yace "Shin ni ne kike so ki kira zakara a fakaice ko me? Amna miye na damuwa dan kin haihu sau uku a cikin shekaru hud'u? Haihuwar ince ba Allah bane ke bayarwa ba?" Kamar za tayi kuka ta kalleshi tace "Eh hakane yah Ammar, amma kuma ai ana so a d'an huta, ka dubi su Alhaji fa ba suyi wayo ba har yanzu. Saida ya gyara tsayuwa yace "Amna ince dai ni na miki cikin?" D'aga kai tayi alamar eh, d'orawa yayi da "Kuma ni zaki haifa ma yaran ko?" Nan ma kai ta d'aga sannan yace "To indai nine uban ina son kayana, ko duk wata ne ki bultso min su zan karb'a, duk wanda kika ga ya miki kallon rashin mutumci kallon daya nuna ana mamakin haihuwarki, to ki kalli k'wayar idon mace ki fad'a mata duk macen da mijinta ke sonta ita ke rirritsa." *To fa kunji wanda basa son haihuwa* Cire kayan jikinsa ya fara yi zai shiga wanka yana fad'in "Ke ba ma dan baki da hankali ba sakarya ce ke, to miye na ki na damuwa ke da bake kika ma kanki cikin ba, ba saida na tab'a ki ba sannan kika yi cikin, wacce miji bai damu da ita ba zai tab'ata ne, yanzu fa da a shekara hud'un nan bamu samu haihuwa bane saiya zama tashin hankali har ana nuna mu da baki, a'a ka na daddage nayi cikin shima sai an min uya shege da buru-uba, to naje nayi d'in kiyi abinda za kiyi idan kin isa." Ban d'akin ya shiga tana ganin haka ta fito daga d'akin bata zame ko ina ba sai b'angaren Hajia, dan in ta zauna ya fito ma d'orawa zaiyi har jarabar ta motsa ya tattausheta a banza, dan yanzu ya fad'a mata ba duka ba zagi amma taji a jikinta, ita kuma a yanda Allah ya halliceta har tafi son dukan ma kan irin wawurar daya mata wani lokaci wacce ta kwana tana amai ga zazzab'i, duk da dai tasan yafi ta ma damuwa da kanta indai aka ce tana da ciki ko tana shayarwa, tanan b'angaren kam sai san barka. Ai kam dai kamar yanda tayi tunani ne, dan ko da ya fito da masifar ya fito yana fad'in "Ke ni ban ma yarda dake ba, wallahi sai kin fad'a min ni ne ba kya so ko yaran ne kike bak'in cikin haifa min, in kuma raino da shayarwa ne baki iyawa fad'a min na ji." Shirun da yaji yasa ya d'auka ko tana falo, haka ya fito da towel d'in niyyar shi in tayi wasa ta sha matsa, amma sai bai same ta ba, murmushi yayi ya jinjina kai yace "Wato ta bar min gidan ma gaba d'aya ko, ga dodo wanda baisan ciwon kansa ba, ga mahaukaci idan nayi na gaji na bari kenan." Komawa yayi ciki yayi k'wafa yace "Zaki dawo ai zan ritsaki ne." *Sati uku* ya rage bikin Hamna, yau kuma ta tashi da shagalin bikin k'awarta da ita ma zatayi aure, ta shirya ma bikin sosai saboda a cewarta shine fitarta na k'arshe kafin ta fara gyaran jiki, d'aya daga cikin abokan Ammar ne na gaban goshinshi zaiyi mata ta biyu, dan haka babu abinda bai shirya halarta ba shima dan saka mishi da alkairin daya mishi. Rana ta farko anyi k'umshi, ta ganshi ya ganta sanda suka je d'aukar abinci, amma kai ka rantse wasu abokan hamayya ne dan babu wanda ya nuna yasan wani ma, a daren ranar akayi kamu inda aka rak'ashe sosai, ya kalleta yafi sau cikin carbi, tana wahalar da zuciyarshi sosai, tana gigita lissafinshi, tana sage mishi duk gwiwoyinshi, yana kishinta fiye da hangen mai tunani, yana jin zafin ganin tana bayyanar da abinda ya kamata ace ta mayar dashi sirrinsa shi kad'ai, sai dai babu ta yanda zai fahimtar da ita haka, baisan ta wace hanya zai bi ya nuna mata yafi kowa son ganin ta killace kanta, amma ya zaiyi da abinda yafi k'arfin wuta inji kishiyar k'onanniya, ya zuba mata ido tayi abinda take so, ko ba komai ma ai ta kusa zama ta wani, mallakin wanin shi ce ita. Anyi bridel a rana ta biyu inda yan mata ne zalla da amarya, sai kuma rana ta uku da angaye ne suka shirya tasu didimar, ya jima da shiryawa ya fita saboda kai da kawonshi yawa gare shi, lokacin da suka zo yana k'ofar gidan da ake gwangwajewar tare da wasu abokinsu suna shigar da ruwan roba ciki, yana juyowa motarsu ta danno wajen, ta glishin motarta ya fara hangosu suna fitowa daga ciki, su hud'u babu mai k'asa da shekara ashirin da biyar a cikin, sun rik'a sun tumbatsa sai haniniya suke🙈, in ba wanda yasan su ba kai kace ba girman garin musulmi bane, dogaye riguna ne duka jikinsu iri d'aya, kalar pink ce sai yar kwalliyar da aka musu a tsakiyar k'ugun rigar, sun kama su sosai a jiki sun fito da duka hallitinsu, dogayen takalmi ne k'afar kowace sai k'ananan poshet a hannayensu, biyu daga ciki haka suka zuba atach d'in babu kitso babu d'an kwali, Amie kuma kitso ne na atach mai kamar na roba, sai Hamna dake da korde a kanta kitson yayi kyau sosai, kallabin Amie a hannunta yake ta rik'e, Hamna kuma ta d'an d'aura shi ne tsakiyar kan wanda kamar jira yake a tab'a shi ma ya b'are, dukansu sun sha uwar kwalliya mai d'aukar hankali. Har sun fara d'aukar hotuna ko da ta ganshi sai kawai ta shige ita ma, Amie ce ta zo kusanshi tace "Namijin duniya barka." Juyowa yayi ya kalleta yace "Barkanki." Yana fad'a ya wuce ciki shi ma ya barta, bin bayansu tayi suka shiga ciki, anata shagali ba kama hannun yaro, kowa na farin ciki da dariya amma banda shi, kujera ya samu ya zauna ya buga tagumi yana kallonta, rawa suke tare da k'awayen inda angayen ke musu lik'i suna jin dad'in kallonsu, jikinta ya bata yana kallonta shiyasa ma bata yarda sun had'a ido ba, shi kuma yana mamakin yanda take son zama, ke da za ayi aurenki amma gida suka bari ta fito, wannan wace irin rayuwa ce akayi a gidan nan? Tab'e baki yayi alamar ba ruwanshi matsalarsu ce. Mutum mugun icce (ina yawan fad'in haka), duk abin alkairi sai wani ya kawo cikas, daren yau dai ko da Hamna ta dawo gida ta riski tashin hankalin da bata tab'a tsammaninshi ba, jin kunya tozarci k'ask'anci duka taji a wannan rana, sati uku ya rage aurenta amma yau an turo manya daga gidansu Habib wai an fasa, abun takaici shine wai mahaifinshi yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _60_ Wai babanshi yace "Sai dai in bayan ranshi zai aureta, amma da ranshi dai har abada kam." Habib fa abun bai masa dad'i ba, amma danginshi da matarshi su abun ya musu dad'i, a ranar haka aka kwana ana jajanta wannan magana kowa na fad'in albarkacin bakinshi, kowa yana son gano bakin zaren dan yaji dad'in fad'a, Amna kwana tayi tana kukan fasa auren yar uwarta, amma ita Hamna ko a jikinta dan sai taji wani sanyi ma. *Da safe* bayan ya dawo daga d'aurin aure ya shigo falon dan gaishe da Ummy, Soueiba Zeinabu da Hassana ya samu suna hirar abinda ya faru, abun mamakin kuma kowace hasashenta take fad'i wanda ya janyo fasuwar auren nan, shigowa kawai yayi bai kulasu ba, saida ya gaisheta ya fito ya gaishe su ya fita, zai nufi b'angarenshi ya kira wayar Amar, yana d'auka yace mishi "Har yanzu kana cikin grp d'in ahalin gaga?" "Eh." Amar ya fad'a a tak'aice, d'orawa yayi da "Ka fad'a musu akwai taro gobe a gidan margayi Alhaji Suley, idan mutum ba zai samu damar zuwa ba ya turo wanda zai iya wakiltarshi." Da sauri Amar yace "Taro kuma? Na me?" "Kayi abinda nace." Yana gama fad'a ya kashe wayar, kamar yanda ya fad'a haka Amar yayi, ya kira taron da babbar murya inda kowa ya amsa da zai zo, kowa tunaninshi da hasashenshi bai tab'a hasaso mishi abinda Ammar d'in ke shirin yi ba. *K'wansu da k'wark'watarsu* haka suka taru amma banda yara, d'akin ya kaure da hira kowa na jiran yaji abinda zai masa dad'i, yasan kowa zai zo shiyasa ma yake kwance yana shan baccinshi hankali kwance, cikin abokan wasansu ne wata ta kalli Amna tace "Wai ke ina wannan d'an rainin hankalin ne? Ko kuma gadinshi zamuyi ne?" Cikin murmushi Amna tace "To miye a ciki ma idan kunyi gadin na shi? Ai ya isa har ya batse." Cikin uwaye ne wata tace "Ki dai taimaka ki nemo mana shi tunda ance yana ciki bai fita ba, muna da abunyi nan da kike ganinmu." Mik'ewa tayi tace "To bari naga idan zan iya." Fita tayi tana tunanin kalar mutanen da zata samu sun hau kanshi yau idan ta tashe shi, sun dai kwanta lafiya lau, amma yanzu zata iya tashinshi ya burma mata ashar yace waya aiketa? Wani iska ta furzar data tuna ai gata zai mata idan ita kad'ai ma ya kunyatar d'in, ko da ta shiga har d'akin na shi ta wuce, yanda ta barshi haka ta same shi, a hankali ta k'arasa ta kwanta bayanshi tana shafa bayanshi, ta jima haka kafin tasa harshenta cikin kunnenta tana karkad'ashi, a hankali ya fara motsa kanshi tare da mimmik'e k'afafunshi, juyowa yayi idonshi rufe ya k'ara matseta jikinshi, ganin abinda take mishi yana ratsa shi sosai yasa ta cire harshenta ta kalli fuskarshi tana murmushi tace "Barka da safiya." Kallonta yayi ya k'ara matsota kusa dashi ya fara sinsinar wuyanta yana shafa bayanta har ya zura hannunshi cikin rigarta, a hankali taji ya fara b'alle bras yana son kaiwa wani wurin, rik'e hannunshi tayi ta kalleshi tace "Duniyata bak'inka fa sun iso tun tuni kai kad'ai suke jira." Lumshe ido yayi ya jawo kanta ya rad'a mata a kunne cewa "Je envie de toi chérie." Kallonshi tayi tana dariya tace "Daga tashinka daga bacci?" Turo baki yayi yace "Ce toi qui ma attaqué." Murmushi tayi tace "Ok, yanzu ka tashi ka shirya sai mu tafi." Ajiyar zuciya ya sauke ya tashi zaune, sauka yayi daga kan gadon ya d'auki doguwar rigarshi fara tas ta saka, turare ya fesa kafin yaja hannunta suka fita, cikin takon isa da mulki da izza dake nuna wannan yaron na Hajia ne ya shigo😂, murmushi yayi ganin cikin k'ank'anin lokaci wai suka taru haka, bai gaishe da kowa ba ya tsallaka ya zauna kujerar da Hajia ke zama kasancewar bata fito ba saboda hayaniyar mutanen, kamar tasan da zuwanshi kam sai gata ta fito, kanshi tayi gadan gadan dan son zama kan kujerarta, gyara zama yayi ya shige cikin kujerar sosai ya d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana shafar gemunshi da hannu, ko da Hajia taga haka kawai tayi shataletale ta zauna kusa da su Hassana da Husseina, dan tasan in tace ya tashi zai fad'i wani abu ne da zaisa a mata dariya, kowa kallonshi yake cikin rashin mutumci da jin haushi, saida ya gama kallon kowa ya d'ago daga jinginar da yayi yana kallon kowa. Cikin taushin murya da girmamawa yace "Barkanku da safiya iyayena kakanni na da yayuna da k'annaina na kaina." Wasu tab'e baki sukayi suna tunanin abinda ya tarasu ya fad'a musu kenan ko me? D'orawa yayi da "A yanda nasan danginmu da gulma da jin dad'in yad'a labari nasan izuwa yanzu kowa yasan abinda ya faru jiya na fasa auren yarinyar nan, to akan shi ne dama zamuyi magana." Kallon kallo suka wa junansu tare da k'ananan maganganu na abinda ya fad'a wai gulma, ba tare da damuwa ya d'ora da "Naji da kunnuwa na na gani da idona a cikin gidan nan masu cewa wai an fasa aurenta saboda hanyar data d'aukarwa kanta marar b'illewa, da jimawa a cikin gari naji da kunnuwana masu zaginta da aibatata, kuma maganar ta samu matashiya ne daga cikin gidan nan, da ku ahalinta ake zaginta a cikin gari saboda shigarta, mu'amularta da k'awayenta, amma abun tambayar anan su waye silar lalacewarta? Su waye sanadiyar rugujewar aurenta?" Tsit kowa yayi sai zuba masa ido da akayi, Hamna kuma dake zaune kan kujera tare da Amna da Umaimah ne ta kalleshi tace "Malam, duk yawan mutanen wurin nan sai akai na ne kawai zakayi maudi'inka." Ko kallonta baiyi ba kamar baisan da hallitarta ba ya ci gaba da cewa "Kune silar komai wallahi." Alhaji *Mani* ne yace "Ya zaka ce mune sila kuma? Yarinyar da take ganin ta waye tana da ilimi da kud'i." Cikin jin haushi Hamna ta mik'e ta kalleshi tace "Na zauna ne saboda yan uwana dana gani amma ba dan jin shirmenka ba." Juyawa tayi zata fita ya kalli kowa na wuri yana murmushi yace "Kun gani, babu wanda yayi yunk'urin yi mata magana kan abinda tayi yanzun, kai tsaye ta nuna ni mashirmanci ne kuma zaman nan baida anfani, bata duba kasancewata babba a gareta ba, hakan bai isa a gareku da zai zama dalilin da zaku tsawatar mata ba." Mik'ewa yayi tsaye yace "To ku saurara, dalilin had'uwar nan ba wai saboda ita bane, wani babban kuskuren mu ne na ke so na tunatar daku shi dan ku gyara, idan kuma baku gyara ba ni dai Allah ya gani kuma ya sani na tunatar daku, tunda a cikin nan akwai wad'anda zan iya musu fad'a, akwai wanda na isa na d'auki bulala na zane su, haka kuma akwai wad'anda ko kallon da bai dace ba zan iya musu ba." Cikin misaltawa da hannu yace "Naji zafi sosai har zuciyata sanda nake tsintar k'ananan maganganu a cikin gari cewa Hamna wai tana abinda take so, daga cikin gidan nan ban tab'a gani ko jin ance anga wanda ya tsawatar mata ba, ban tab'a ganin wanda yace mata ta canza shiga ko kayan jikinta ba, a cikin gidan nan ma babu wanda ya damu da ita bare kuma daga waje, kuma abinda na lura ya jawo hakan ba zai wuce wariyar launin fatar da ake nunawa ba, wai yau lalacewar ahalin nan ya kai matsayin da kowa nashi kawai ya sani, babu wanda zai iya kallon d'an dan uwanshi ya mishi magana ko fad'a kan abinda yayi bai dace ba, kowa yafi son ya tsaya daga nesa yana nuna d'an uwanshi da baki, wannan wace irin rayuwa ce?" Husseina ya kalla da Hassana da Hajia yace "Kune manyan da suka rage mana a ahalin nan, kuna da dama da iko a hannunku yanda zaku iya tank'wasa duk wani k'aramin tsagera, saboda kuwa ku kuka haifi iyayenmu, amma me kukeyi dan gyara iyalin nan?" Matse bakinshi yayi yace "Kowa nashi yaja ya killaceshi a jikinshi yake bashi kulawa, d'aya ba zata iya iya tattaunawa akan matsalar data shafi d'aya ba, ko da na tashi a gidan nan cikin sauk'i na fahimci wacece kakata wacce ta haifi mahaifina, wanda ba haka ya kamata abun ya zama ba, yanda gidan nan ke da girma da mutane ya ci ace yaro zai sha matuk'ar wahala kafin ya gane mahaifiyarshi ma bare kuma kaka." Kallon Husseina yayi yace "Bansan asalin meye tsakaninki da Hajia ba, amma yanda ke ma kike nuna baki damu da al'amuran 'ya'yanta ba abun babu dad'i, sanin kanki ne Alhaji baya nuna banbanci tsakanin wanda suke nashi da wanda suke na yan uwanshi, amma a gaban idonshi duk wani al'amari daya kamata kiyi magana saiki zuba ido kina kallo, saboda a ganinki ai ahalin Hajia ne ke kuma ba kya son shiga sabgarta, amma ya ci ace kina yi ko dan d'an uwanki." Sauran mutanen ya kalla yace "Yau da kuka ga yarinyar nan akan titi cikin shigar da bata dace ba, kowa na da iko da hujjar da zai iya mata d'an banza duka, kuma babu abinda zai faru duk inda za aje, ku dubeku kuma da kuke gida d'aya, kuna sane da duk rashin mutumcin da take amma kuna kallo, ba komai ya kawo hakan ba sai dukanku kowa yana ji cewa ba ciki d'aya suka fito da ita ba." Yayi maganar ne yana nuna su Amar da hannu, d'orawa yayi da "Dukanku nan babu wanda baya zarewa k'anninsa ido wanda suka fito ciki d'aya, amma wanda suke yan uwan juna kuma duk abinda yayi sai ka kalleshi da ido ko ka nuna baiyi laifi ba." Juyawa yayi ga lieutenant da Ummy yace "Tanti Hadiza data baku amanar yaran nan ta baku ne da tunanin zaku tarbiyancesu kamar yanda ita ma zatayi, bakuyi laifi ba da kuka nuna musu soyayya har baku ganin laifinsu, amma kun kasa gane abinda ke daidai dasu da wanda ba daidai bane, kunfi kowa sanin tanti mace tsayayya da jajircewa kan abu, mace ce ita da bata yarda da raini ko shashanci ba, domin kuwa a rashin son wannan abubuwan ne ma yasa yau bata gidan nan, saboda ta k'i yarda a mulketa da ranta da lafiyarta, me kuke tsammanin zata ji idan taji an fasa auren 'yarta? Musamman ma taji dalilin fasa auren." Hajia ya kalla yana murmushi yace "Hajia, Hajia, Hajia, nasan nan da zan bawa kowa dama ya fad'i dalilinsa na yin shiru, to kowa zai ce ne ke ce baki bayar da damar shiga hurumin iyalinki ba, suna da gaskiya ta wani b'angaren, amma ni dai a gani na ba hujja bace da zata sa kowa ya k'yale kuma yana ganin ba daidai ba, Hajia bansan me ye a kanki ba, amma ni dai kina birgeni, saboda jajircewarki da tsananinki kan iyalinki ya taka muhimmiyar rawa wajen hana faruwar wasu abubuwan, daga sanda kikayi shiru kuma sai komai ya fara lalacewa, matsalar d'aya ita ce ba kya jan iyalinki a jiki ta yanda zasu saba dake, idan akwai sabo tsakaninki dasu zasu iya fad'a miki komai daya shafesu babu tsoro, amma tsoron nufo ki ma Hajia yana gigita wasu, wasu duk maganar da zasuyi sai sun anbaci sunanki da cewa kar a ja musu matsala, misali Ummy na." Ya fad'a nunata da hannu ya d'ora da cewa "Ita ce surukarki ta farko a gidan nan kuma matar babban d'an ki, a k'alla yanzu tana da shekara talatin da shida a gidan nan, amma wannan shekarun basu sa ta samu kusanci dake ba, har yau har yanzu bata iya kallon cikin idonki ta fad'a miki abinda ya dace da ita ko ya'yanta, uwa ta kan sadaukar da komai nata akan yaranta, amma banda Ummynmu, a jimawarta gidan nan ta kai matsayin da zata iya zartar da hukunci kuma ya yanku, amma har yanzu zuciyarta rawa take idan tana tare dake, jikinta b'ari yake idan tana magana dake, hakan ne yasa ta b'oye miki al'amari mai girman gaske wanda ya kamata ace kin sanshi, da kin nuna ita 'yarki ce data fad'a miki ko da ba zaki ji dad'i ba." Dukansu ya kalla yace "Rayuwar nan bata da anfani idan ba zaka anfani d'an uwanka ba, ya kamata mu san yanzu mun rasa dattawan da suka rage mana, dukanmu yanzu anan mu ne muka rage ma junanmu, mu rik'e zumuncinmu kar muyi wasa dashi, mu kula junanmu kamar yanda zamu kula wanda muka fito ciki d'aya dasu, idan haka ta kasance wallahi ba *Ammar* marar kunya da rashin tarbiya d'aya za'a samu ba, za'a samu wasu Ammar d'in ma, sannan marasa jin magana ire iren yarinyar can..." Ya fad'a yana nuna Hamna dake tsaye inda take yace "Indan har Ammar baiyi magana ba Amar zaiyi, idan Junaid baiyi ba Jibril zai tsawatar, idan Jamil baiyi ba akwai Abdul Rashid, in basu min magana ba akwai *Nura* akwai akwai akwai...etc, dole yara zasu gyara su kimtsu, dan in baka had'u da wane akan hanyarka ba zaka had'u da waninshi." A shek'e ya kalli kowa yace "Yanzu ma nasan akwai wanda zasu ce na tarasu ina musu rashin kunya da fitsara, to ku gafarce ni duk wanda na b'ata masa rai, kuma nayi mamakin zuwanku haka da gaggawa, watak'ila kun d'auka wata dukiyar ce aka sake ganowa da Alhaji ya bari, shine kowa ya zo d'aukar nashi kason, ba'a d'auka ni na kira taron ba." K'arashe maganar yayi da dariya, magana ta gaskiya akwai wad'anda a lokacin suka ji yaron ya birgesu, dayawa daga ciki abu ne da yake ci musu tuwo a k'warya, amma sai gashi yayi magana ya tab'o kowa. Gogan kam Amna ya kalla ya mik'a mata hannu, Amna da taji soyayyar mijinta ta sake huda zuciyarta cikin murmushi ta mik'o masa hannu ya kamota, saida ya kalli kowa yace "To ku rufe da salatin annabi, Allah yasa mu dace." Amna ya kalla yace "Duniyata muje ki sauke ni, a sama nake wallahi." Ta gabanta suka wuce inda kowa ya bisu da kallo, numfashi kawai kake ji na fita a wurin, sun jima zaune haka kafin Hajia ta sunkuyar da kanta tace "Kuyi hak'uri, yayi maganganu da dama a wurin nan, amma duka nice mai laifi saboda ni ce ban bayar da fuskar da za'a shiga shirgin iyalina ba, ba nayi haka bane dan bana so a rab'eni ko zuri'ata ba, kawai dai ina so ne naga tawa zuri'ar ta banbanta data kowa, ina so naga babu mutanen kirki irinsu, amma ban tab'a tunanin hakan zai zama matsala da zai iya kawo rabuwar kai ba, ku gafarceni dan Allah ku yafe min." Alhaji Mani ne yace "Kamar yanda yaron nan ya fad'a ne Hajia ba laifinki bane ke kad'ai, mgana ta gaskiya mu ma muna da laifi, tunda ko baki so zamu iya magana amma muka yi shiru, amma yanzu dai tunda k'aramin yaro ya d'ora mu a hanya sai a yafi juna a kuma gyara gaba." Su Hassana da jikinsu yayi sanyi ne yace "Allah ya yafe mana baki d'aya." "Ameen." Aka amsa dashi duk d'akin sai kuma aka kwashi hira, Zeituna ce ta mik'e tare da su Shafa'atu tace suje to a d'ora girki, tunda an riga da an had'u kafin kowa ya tafi, madafa suka nufa sai mazan da suka fita waje, a wannan taro na wannan rana wanda Ammar ne silarshi har suka d'ora zubin kara wanda musababbinshi had'uwa ce ake son a dinga yi duk wata, ba'a fitar da yan mata ko yaran mata ko tsofaffi ba, duk mai so ne wanda ya ga zai iya duk wata, babu wanda ya yarda aka barshi a baya duk da za'a dinga zuba kud'i, amma a lokacin abun ya shiga zuciyar kowa ba kud'in ne abun dubawa ba sai girman zumuncin da za ayi. *A dole* ta gyara ba dan tana so ba, 😂(rubdugu) rubdugun da akayi akanta kad'ai yasa ta d'an saya shigarta, hatta su Amie ta daina yarda yanzu su zo gidan nan sai dai su had'u a salon d'inta, amma a haka wata rana Amie na zuwa amma bayan ta sako hijab. *Bayan wata biyu* Hajia ta tisa k'eyar Hamna da Amna Umaimah dasu Jamila suka tafi hadj, wanda tafiyar Amna ta bawa mutane mamaki sanda aka ji ta tafi da ciki, lafiya sukayi aikinsu suka gama suka dawo lafiya, har yanzu ba wani hijab take fita dashi ba, sai ma uwayen rigunan data kwaso tafiyarsu masu kyau, kusan yanzu su tafi sakawa indai ba gida ka sameta ba ka ganta da riga da siket ko da zani. Yau ma tsaf ta shirya ta tafi wani babban mall dan siyayyar abin buk'atarta, ta shiga tana cikin duba abinda take so kawai suka had'e da Habib. Kallon da yake mata yana tunanin ya mata magana ko kuma ya k'yaleta, shi fa ko yanzu aka yardar masa zai aure ta, amma ganin irin kallon da take masa yasa shi kallonta kawai shima, wucewa taje yi ta gabanshi sai kuma hanyar ta d'an matse, karkatawa tayi zata wuce ta kalleshi tace "Malam zan wuce." Mamaki ta bashi ganin yanda ta nuna kamar basu tab'a sanin juna ba, kauce mata yayi a hanya zata wuce yace "Hamna abun ba ko gaisuwa?" Kallonshi tayi ta wurga masa harara taja tsaki ta wuce, da kallo ya bita duk sai yaji babu dad'i, tana gama abinda ya kawota ta juya ta tafi, a hanyarta ta komawa ta had'u da Alhaji *Sabi'u*, babban shahararren d'an kasuwa, babban mutum ne mai iyali da tunbi😂, sanda suka tsaya bakin madakatar danja a lokacin ya sakar mata na mujiya, ba mutumin kirki bane ko kad'an, indai zaiga mace to fa babu lafiya hankalinsa tashi yake, binta yayi a baya har ta isa gida, gira d'aya ya d'aga sama ya cije leb'e sanda yaga gidan data shiga, lallai ko giyar wake yasha bai isa ya tunkari gidan nan da sunan zai wa yar gidan lalata ba, yana da sani sosai akan mutanen gidan, kama daga gwamnansu Gambo, lieutenant na douanes da kuma colonel na soja, kai ba ma zai yiwu ya fara ba wallahi indai yana son kansa da mutumci, amma kuma ya gani yana so saiya kenan?. *Bari Fan's badak'ala su fad'a maka yanda zakayi? Ni ma idan kuka min comment saina baku wata page muji me zaiyi*. *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _61_ Maganar aure ya shigo da ita dan ya samu abinda yake so, mutum ne dake iya b'atar da ko nawa ne dan ya samu biyan buk'atarsa, ita bata sanshi ba dan ko ganinshi bata tab'a yi ba, wani shu'umin mutum ne daya san kan tsiya kowace iri, kai tsaye gidan ya fara zuwa ya gabatar da kanshi ga manyanta, saboda kowa yayi karatun tanastu yasa Hajia da kuma lieutenant cewa sun gamsu da kamalarshi, daga yanda suka mata magana ya nuna umarni ne suke bata data aure shi, abinda ta fad'a musu kawai shine "Allah ya zab'a mana mafi alkairi. A ranar da ya zo dan su fahimci junansu data ganshi saida ta tsorata, zuciyarta ta tashi sosai saboda ba wai muni ne fa shi ba, gashi da tsayi da babban tunbi, sannan bak'i wulik dashi sai idon kwartaye🙈, da k'yar ta iya gaisawa dashi kafin tace zata koma bata jin dad'i, Ammar ne ya shigo farfajiyar b'angaren Hajia zai shiga falon yana d'auke da Ameera a kafad'arshi, saida gabanshi ya fad'i daya ga wanda take tare dashi, me ya had'ata da Sabi'u kuma har gidansu? Yana k'arasawa bai kalleta ba ya bashi hannu yana fad'in "Alhajin Allah kaine a gidan mu?" Wuk'il wuk'il yayi da ido dan duk jikinshi ya mace ya sare da al'amarin yarinyar, yaji a jikinshi wannan ita ce yarinya ta farko data birgeshi kuma bai samu biyan buk'ata ba, dan shi sai yanzu ne ya tuna ashe wannan pand'ararren ma a gidan nan yake, to shi ina zai iya da jarabar bawan Allahn nan, yo shi ko baya da iyali ai zai k'wauracewa kwatirarsa bare kuma yana da wanda baya san sa su a matsala. Da k'yar ya bashi hannu yana fad'in "Alhaji Ammar kana lafiya." Ta gefen ido ya kalleshi yace "To lafiyar nan dai da dama, jiya ai nayi croisement da kai a babban titi." Kallonshi yayi da mamaki dan shi dai yasan jiya duk a yawace yawacen shi bai isa can wajen ba, cikin k'yabta ido na marar gaskiya yace "Wane lokaci?" Cikin murmushin mugunta yace "Nasan dama baka ganni ba, amma ni na ganka tare da wata cikar, da farko ma na d'auka madame ce wallahi, sai daga baya na ankare ashe ba ita bace, ai na so tsayar da kai dan ni kaina kayan sun birge ni fa, kai Alhajin nan ka iya zab'ar harka." Ko da ya gama fad'a kuma ya shige yana mishi dariyar mugunta, kawai ya fad'i hakane fa dan ya ankarar da ita in ma bata san waye ba, in kuma ta sani to tasan da irin mutumin da take mu'amula, kallonshi tayi sai taga kawai yana ta zufa, da k'yar ya kalleta yana washe mata baki, yamutsa fuska tayi tace "Saida safe." Da kallo kawai ya bita, tana shigewa ya mik'e ya kalli k'ofar ya nunata da hannu yace "Wannan Ammar wannan Ammar Allah ya tsine maka albarka, shegen yaro mai kama da kafiran farko." Juyawa ya fita ba tare da tunanin sake dawowa ba, ita ma ko da ta shiga bata iya cewa komai ba kawai ta zubawa sarautar Allah ido, su Jibril kuma dake fita su suka samo cikakken bayanan shi, dan haka ana jin waye shi aka ce wannan magana ba ita ba kamarta, tayi farin ciki saboda ta tsira daga wannan tullu, *bayan wata d'aya* kuma Allah ya sake had'ata da d'an abokin lieutenant, shima dan danan magana ta kankama har an saka ranar kawo kaya, sai dai shi kuma matsalar ance matarsa ce fitinanniya namber one, dan a cikin gida ma ita ke mulki, lieutenant ne yace baya son tashin hankali dan haka Allah ya fito mata da wani. *Sanda* ake ta k'ok'arin ganin an had'a Hamna da wanda ya dace, a lokacin kuma Amna taje awo na farko, a cikin tambayoyin da likitar ta mata ne take tambayarta bata jin wata matsala, cikin sanyi jiki tace "Gaskiya ina d'an yawan jin ciwo haka kamar kusan k'uguna da...mtsss ni abun ma wallahi ya fara damuna." Tambayarta tayi "Kina jin zafi idan kina fitsari?" Da sauri tace "Gaskiya ina ji, na jima ina jin haka kad'an kad'an." "Kina zubar da farin ruwa ne masu kamar kub'ewa?" A hankali tace "A'a." "To akwai kasala ko ciwon jiki?" "A'a." Shima ta fad'a, ci gaba tayi da rubutu tana mata tambaya kafin daga bisani ta rubuta mata wata takarda ta bata tare da cewa "Ki samu rendez vous kiga gynécologue saiki masa bayanin abinda kike ji, insha Allahu idan ma magani ne ko shawarwari duk zai d'oraki akai." Tunda taji abinda ta fad'a gabanta ya fad'i, a take jikinta taji yayi mugun yin sanyi, sai taji duk ta sare hankalinta da nutsuwarta suna neman barinta, a daddafe aka gama mata awon nan ta dawo gida, daga Ummy har shi babu wanda ta fad'a ma, tunaninta kawai shine idan taje taga docteur d'in za'a jawo mata ciwon da bai kai girman matsalarta bane, dan haka taja baki tayi shiru bata fad'a ma ko da yer uwarta ba, sanda ya dawo gida saida ya tambayeta ya awonta ya kasance, amma sai tace lafiya lau, a haka aka tafi da lafiya lau ta ci gaba da b'oyewa, saida lokacin komawarta awo na biyu yayi ta samu tayi d'ibar jini shi ma dan tasan sai dashi za'a mata awo na gaba, ko da taje asibitin ta kuma yi sa'a da likitar data dubata a farko ta tambayeta me aka ce mata, sai kawai tace ai ta daina ji ma da aka d'orata kan magani yanzu ta warke, anan likitar ke mata murna dan ita kanta da taji ta fad'a mata abinda take ji saida ta d'anyi wani tunanin na daban. Duk zaune suke a falo sun gama shirin tafiya barka gidan Nura da matarshi ta haihu, kusan duk jikokin nan yanzu Hajia ce ta d'auki nauyin yin kayan barka indai akayi haihuwa, hakan ya ma kowa dad'i inda addua'r sa albarka ke riskar Ammar kowane lokaci, dama tace sai zasu tafi sai su biya a siye kayan a wuce, Zeituna ce ta kalleta babu fargaba babu tsoro cikin farin ciki tace "Hajia dreba fa na jira a waje, kuma gashi baki fad'i me da me za'a siya ba." Kallonta Hajia tayi ta kalli Ummy dake b'allawa Shureim botira tace "Ga Sa'ada nan ta fad'a miki duk abinda ya kamata saina bayar da kud'in a siya." Kallonta Ummy tayi ido ciki ido babu wannan sunkuyar da kai ko wani abu tace "Idan mun tafi zai sauke mu tare ai sai mu siya." Jinjina kai tayi ta kalli Husseina tace "Kiyi sauri ke kuma ki gama shafa kwallin nan kamar wata budurwa kike ta darzashi a ido." Saida ta murgud'a mata baki tace "Babu ruwanki barni na shafa, kika sani ko na samu miji daga wannan fitar." Dariya Hajia tayi tace "Ai kuwa dai zai kwashi kabari kusa." Kallonta tayi tace "Au! Ke a ganni zan mutu da wuri ne? Ai ko zan tafi tare dake zan tafi, kuma ma ai kin fini kusa da kabarin." Cikin dariya Hajia tace "Saboda me?" "Saboda ke ce mijinki ya mutu." Ta fad'a tana mik'ewa tana gyara gyalenta, su Zeinabu dai dariya suke har suka rungud'a baki d'aya suka fita, lallai rayuwa yanzu ta sauya sosai. *Bayan sun dawo* da dare ana zaune ana ta hira gwanin sha'awa, colonel ya diro garin cikin kakinshi marar hayaniya sosai sai tarin galolin nasara da jajircewa, har gabanta yaje zai durk'usa ta rik'e hannunshi da murmushi a fuskarta ta zaunar dashi gefenta, fuskarshi take kallo tace "Hussein an dawo lafiya? Ya aikin kuma?" Saida ya kalli su Ummy da Zeinabu dake gefe, shi dai baya nan aka samu wannan canjin, hakan bata tab'a faruwa ba sai yau, cikin ldabi yace "Hajia kuna lafiya?" Cikin murmushi tace "Lafiya lau kowa." Dafashi tayi tace "Ka shiga ciki ka samu kayi wanka sai ka zo ka ci abinci ko." Sunkuyar da kai yayi yace "To Hajia, nagode Allah ya k'ara girma." Da murmushi ta amsa da "Ameen, Allah yayi albarka." Shigewa yayi ciki yana jin wani sakai a zuciyarshi, ita kanta yanzu wani sakayau take ji data zama mai bin yaranta da addu'a, duk sanda ta musu sai ta ga tsantsar farin ciki a fuskokinsu, yanzu da take jan kowa a jikinta sai taji tafi ingantacciyar lafiya, bakinta baya zama shiru, yara duk suna sakewa da ita har su zauna gabanta suna hira ko da ta shirme ce, yanzu har basa zama falonsu na sama sai falon tara da ita, kuma a wannan zaman da take tare da su ne take gyara musu wasu k'ananan kurakurai ko da na cikin fad'a ne a kalma, lallai ta jima tana rayuwa cikin kuskure. *Rayuwa kenan*, a cikin wata hud'un nan sau uku ana d'auko maganar auren Hamna amma sai abun ya lalace, izuwa yanzu kam sai kowa ya fara wani tunanin na daban, Husseina da Hassana ne suka mik'e wajen neman taimakon malamai, sai dai duk inda zasu tafi basa tafiya da Hamna sai dai su fad'i matsalarsu kawai, dan Husseina tace ba zata yarda abinda ya faru kanta ya faru kan jikarta ba, da ire iren haka suka fara takura Hamna da turare turare da shaye shayen rubutu da maganin aniya makomiya😂, inda abun ya fara girman da ana sauke Qur'ani da sadaka da yanka abun sadaka, an shiga kashe kud'i sosai saboda tunanin ko sihiri ko kuma aljanu, sai dai har yanzu babu wani labari. *Duk* da ciwon kan da take ji bai hanata kama wankin kayan yaranta ba, dan in suka tafi islamiyya kawai take samun damar yin aiki hankali kwance, duk sanda ta duk'a sai taji kamar kanta zai fad'o k'asa ko idonta, idan ta d'ago kuma saita rintse ido saboda jiri ke d'ibarta, a haka dai ta sake sunkuyawa d'aukar wasu kayan dan ta shanya, tana d'agowa taji kamar an buga mata guduma a tsakar kai, daga lokacin bata sake sanin me ke faruwa a duniya ba, fad'uwa tayi da tsohon cikinta wata takwas wanda aka bata sati biyu idan bata haihu ba ta koma asibiti, bokitin ne ya juye inda ruwan suka malale har suka gangaro inda take kwance suka b'ata ta. Kasancewar yara duk na islamiyya manya kuma basu cika shiga b'angarensu ba yasa ta kwashi tsawon awa uku da rabi a wurin babu wanda ya sani, sai tasowar yara ne daga islamiyya, su Abba da Ameer b'angarensu Ummy ma suka nufa dan can ake basu biscuit da chocolat, Ameera da tafi sarkawhar mahaifiyarta kai tsaye can ta nufa ita ma, ko da taga d'aki rufe ma ta d'auki hanyar da zata sadata da bayan gidan inda suke wanki wani lokacin har su zauna shan iska, ko da ta zagaya ta ganta kwance ta k'arasa, ita dai tasan kwancin nan bana lafiya bane, sai kawai tayi zaune kusanta tana daddab'ata tana kiran "Ummy, Ummy ki tashi k'aca ne fa kika kwanta." Jin shiru yasa ta k'ara girgizata tana fad'in "Ummy bake ke ana mu wacan k'aca ba? Shine kuma kika b'ata jikinki kema, saina fad'awa Papa." Tun Ameera na magana har ta gaji ta d'ora kanta akan cinyarta ta kwanta ita ma ta fara kuka. Shi kanshi Ammar gabanshi yaji kawai yana ta fad'uwa, ya rasa me ke mishi dad'i a duniyar, wayarshi ya d'auka ya kirata da nufin tambayarta yara sun dawo daga islamiyya, saida yayi kira takwas ba'a d'auka ba sai kawai ya d'auki makullin mota ya fito, bai tsaya ko ina ba sai gidan, shi ma yana ganin k'ofar rufe saiya juya ya shiga wajensu Ummy, yana ganin Ameer sun shiga wasa da uniforme d'in su yace "Sarkin k'iriniya ina uwarka take?" Saida ya nuna mishi b'angarensu yace "Tana can." "Ameera fa?" Ya fad'a yana kallon sauran yaran, nan ma nuna masa yayi yace "Tana can." Juyawa kawai yayi ya sake komawa, wannan karan kai tsaye bayan gidan ya nufa, yana dosa ya hangin tashin hankalin da ko a mafarki baiyi tsammanin riskarshi ba, Ameera dake kuka har ta daina saboda baccin daya d'auketa sai ajiyar zuciya take, da gudun bala'i ya k'arasa yana kiran sunan "Amna, Amna, lafiya?" Durk'ushewa yayi ya tallabo kanta, luuuuu kanta yayi yana ta langab'ewa, cikin kid'ima ya kamo wuyan hannunta yayi shiru, da sauri ya d'ora yatsunshi biyu kan wuyanta yana saurare, jin akwai alamar harbawar jijiya yasa shi saurin mik'ewa tsaye, janyo Ameera yayi daga jikinta baiwar Allah a cikin bacci ta firgita ta tashi, bai kula yarinyar ba ya tattaro Amna ya rumgume kamar yar beby yayi waje da ita. Yaran ne suka sanar da fitarshi da Amna, ko da suka fito har ya figi motar sun bar gidan, a tsiyace yake gudu yana juyawa yana kallonta, da hannu d'aya yake tuk'i d'aya hannun kuma ya rik'e nata gam, Allah, Allah, Allah, kawai yake maimaitawa shima a zuciya, komai ya tsaya masa cak ya rasa me zaiyi tunani akai, yana isa bai bari mai gadi ya bud'e masa ba ya fito, mai gadi na shirin bud'e k'ofar yaga mai gidanshi a gigice ya bud'e gidan baya yana k'ok'arin d'auko mutum, da gudu ya shiga asibiti inda ya sanar dasu aka fito da gadon d'ora marar lafiya, yana daf da shiga suka had'e nan ya d'orata suka jata da gudu, ana turata d'akin da za'a dubata sai kawai ya ja ya tsaya, gashi yau asabar Ummy na gida, hannu biyu yasa ya shafi kansa tare da tsayar da hannayen saman kai, likitoci biyu mata ne suka shiga sai d'aya likitan wanda zai shiga ya ga Ammar ya tsaya shima saiya tsaya ya kalleshi, dafa kafad'arshi yayi yace "Muje mana, zamu buk'ace ka a ciki." D'ago duka idonshi yayi ya sauke mishi su, kallo ya bishi da shi kamar bai gane yarenshi ko kuma yau ya fara ganinshi, ya jima yana masa wannan kallon kafin ya bud'e baki yana son magana sai kuma ya kalli gefe, idonshi yaji sun cika da k'walla sai yayi saurin tsayar dasu ya kalleshi, girgiza masa kai yayi yaja baya baya ya zauna dab'as kan dogon bencin k'arfe dake bayanshi, duk'e kanshi yayi ya tangaleshi da tafin hannayenta, ganin haka sai kawai likitan ya juya zai shiga ciki, da sauri ya mik'e ya rik'o rigarshi, juyowa yayi yana kallon sai kuma ya sunkuyar da kai, dafa kafad'arshi yayi yace "Ammar, ka kwantar da hankalinka mana, kai ma fa likita ne, k'warin gwiwa kake buk'ata." Iska ya furzar ya d'ago ya kalleshi idonshi sun rine sosai, cikin amon muryar kuka yace "Dan Allah, dan Allah ka ceci rayuwarta." Jinjina masa kai kawai yayi ya juya ya shige, komawa yayi ya zauna ya dafe kanshi, a hankali yace "Me ya sameta? Me zai faru yanzu?" D'ago kanshi yayi yana dafe da goshinshi yace "Cikin nan karka zamar mana matsala, ta min k'orafi akan shi amma ban ji ba, idan da nasan haka zata faru da tun farko na saurareta mun samu mafita." Kafad'arshi da yaji an dafa yasa shi juyawa ya kalli wanda ke bayanshi, Ummy ce tsaye tare da su Hajia Zeituna Zeinabu da sauransu, da sauri ya rik'e hannun Ummy yace "Ummy tana ciki, bansan me zai faru ba." Kallonshi tayi tace "Me ya same ta?" Kai kawai ya girgiza bai ce komai ba, shiru sukayi kowa na addu'a a zuciyarshi, likitan ne ya fito da sauri da takardu a hannunshi ya zo ya tsaya gabansu, da sauri ya tashi tsaye yana tambayarshi lafiya? Saida ya kalli Ummy sannan ya bashi takardun yace "Muna buk'atar sa hannunka za'a mata aiki dan a ceto abinda ke cikinta." Fad'uwar da gabansa yayi yasa shi dafe k'irjinshi, rik'e hannunshi yayi yace "To ita fa?" Kallonshi yayi zaiyi magana sai Ummy tayi saurin karb'ar takardun tace "Dukansu za'a fito dasu lafiya, saka hannun anan." Kallon Ummy yayi sai yayi murmushi yace "Yawwa Ummy na." Da sauri ya saka hannun likitan ya kalleshi yace "Muna buk'atarka a ciki Ammar, da alama ta d'auki kusan awa hud'u ko uku da rabi a sume, hakan ya jawo tsayawar..." Da sauri yace "Zuciyarta na bugawa?" Kallonshi yayi yace "Shiyasa nake so ka shiga ciki, zuciyarta na bugawa amma ba daidai ba." Da saurin bala'i ya tunkari d'akin ya shige ciki, saida ya shiga ya saka rigar aiki da hula da safar hannaye, rintse ido yayi ya bud'e akan ta, an saka mata oxygène tana kwance kamar gawa, saida ya kalli n'aurar dake nuna bugun zuciyarta da numfashi, nan ya shiga had'a allurai da abubuwan da suka dace, inda d'aya likitan kuma yasa aka mata allurar kashe zafi, nan da nan cikin k'warewa ya farkata inda Ammar ya kasa kallonta a wannan halin, bugun zuciyarta kawai yake dubawa yana fad'awa likitan yayi sauri dan ya samu damar yin nashi aikin shima, ana ciro santalelen yaron ya fashe da kuka, da sauri ya juyo yayi saurin karb'arshi, kallon fuskar yaron yayi sai yaji hawayen da yake ta k'ok'arin b'oyewa sun zubo masa, d'aya daga cikin likitocin ne ta amshe shi ta shiga kula da yaron dake ta tsanyara kuka. Yana gama mata d'inki shima ya shiga dubata, bai tab'a tunanin zai iya nuna k'warewarshi kan wani na shi ba, gashi yana aiki akan matarshi data fara rikid'ewa ta zama jinin jikinshi, yana aiki akan ta cike da son ya ceci rayuwarta ta rayu, yana aiki akanta da niyyar ko tashi zuciyar ce ya cire ya dasa mata, amma kuma hannayenshi rawa suke, tausayinta da k'aunarta sai wahalar dashi suke a lokacin, sai gashi ya kai matakin da ma baisan me yake mata ba, likitan ne ya kula da hannunshi sai rawa suke kamar yau ne ya fara aikin, likitan na shirin dafa shi sai gani yayi ya saki wani d'an tsinken dake hannunshi ya juya baya yana rufe fuskarshi da hannu, da sauri ya matsa kusa dashi da nufin ya mishi magana, ikon Allah sai kawai suka ji n'aurar na kukan dake nuna bugun zuciyar ya fara tafiya daidai. Tare suka juyo sukayi kanta, hannunta ya rik'e yana murmushi yana fad'in "Alhamdulillah, Allah na gode maka." Nan suka gama abinda za suyi aka kimtsata, saida aka d'ibi jininshi aka k'ara mata kafin aka fito da ita d'akin hutu. Yana d'akin tare da ita su Ummy na zaune farfajiyar asibitin, a firgice Hamna ta shigo daga salon da aka fad'a mata, tunda ita dai tasan ba watan haihuwarta bane, Ummy ta kalla tace "Ummy ina Amna? Me ya same ta?" Da dariya ta kalleta tace "Lafiya lau take yanzu, tana d'akin hutu." "Amma Ummy me ya sameta to? Lokacin haihuwarta ai baiyi ba?" Hajia ce tace "Ki nutsu ki shiga ki duba ta, aiki aka mata." Da k'arfi tace "Aiki kuma? Amma ba tana haihuwa da kanta ba?" Zeinabu ce tace "Bari kedai wallahi, wannan ce ta zo da matsala." Da sauri tace "Wane d'aki take?" Ummy ce tace "Tana d'akin da aka kwantar da Jamila lokacin baya." Da sauri ta wuce tana gyara kallabin doguwar rigarta dake jan k'asa, da k'arfi ta bud'a k'ofar ta shiga, da sauri ya kalli mai shigowa ita ma idonta cikin nashi dan bata tsammanin yana ciki, babu wanda ya iya canza fuskarshi daga yanayin alhinin da sule ciki saboda halin da ake ciki, sai tausayinshi ma da taji na ganin idonshi jawur kamar yayi kuka, k'arasawa tayi ta zauna bakin gadon tana kallonta, a hankali ta dafa hannunta mai d'auke da zoben azurfa fari irin na Hamnar, d'an satar kallonshi tayi tace "Ya jikinta?" Cikin muryar jimami yace "Lafiya lau." A hankali Amna ta bud'a idonta, dishi dishi take gani da k'yar ta saisaita ta sauke idon akan Hamna data fi gani da kyau, murmushin k'arfin hali ta mata cikin muryar da bata fitowa sosai tace " *Saboda ke na dawo Hamna*." Da mamaki suka kalli juna ita da Ammar suka kuma kallonta, a hankali tace "Ban gane saboda ni ba? Daga ina?" Ba tare da murmushin nan ya bar fuskarta ba tace "Gidan da ba'a dawowa mana, saboda ke na dawo yer uwa, bana so na barki ba tare dana tafi da sanin kina hannun wanda ya dace ba, sannan ina so na bar amanar yarana hannunki, ko ba komai suna kallon uwa saboda yer uwata ce ke kuma fuskarmu d'aya, dan Allah yer uwa ki samu mai nagarta da kamala wanda zai iya k'aunarki a duk yanda kike kuma har abada kamar *miji na.*" Hawayen da suka taho ma Hamna ne tayi saurin gogewa ta kalli Ammar tace "Me yasa take magana haka?" Dariya Amna tayi har hak'oran makkarta ya fito tace "Ki saurare ni mana." Girgiza kai tayi tace "Kinga kiyi shiru dan Allah baki da lafiya." Mik'ewa tayi zata fita Amna tace "Yer uwa." Tsayawa tayi ta juyo, saida ta lumshe ido tace "Ba zan tab'a damuwa da halin da zan bar yarana ba saboda na bar musu ke." Da gudu Hamna ta fita daga d'akin tana kuka, kallonta yayi ya rik'e hannunta yace "Duniyata kiyi shiru ba'a son magana kinji." Murmushi ta masa tace "Ina so nayi magana da yer uwata yah Ammar." Cike da tabbatarwa yace "Shikenan kiyi shiru yanzu, idan jikinki ya k'ara kyau zan kira miki ita." Wani murmushi tayi mai ciwo tace "Na fad'a maka zan kai gobe ne?" Kafeta yayi da ido yace "Zaki kai insha Allahu har ma ki wuce." Wani murmushin ta sake masa tace "Malam taimaka min na tashi ina so nayi sallah." Saida yayi ajiyar zuciya yace "Kiyi hak'uri Amna, a yanayin da kike zaki iya jinkirta sallah." Had'e fuska tayi tace "Ba ruwanka kawai ka tashe ni nayi sallah, idan na mutu me kake so na fad'awa Allah, idan kuma ba zaka iya ba ka kira min Ummy." Zuba mata ido kawai yayi yana kallo, abinda ya lura dashi kawai zafin aikin da aka mata ne yanzu ya had'e mata jiki yasa take sambatun nan, da taji ya k'yaleta sai kawai ta fara k'ok'arin tashi tana fad'in "Ni banga anfanin zamanka anan ba in ba zaka sani yin sallah ba, kawai ka barni na tashi na gaishe da ubangiji na." Rik'eta ya kwantar da ita yana daddab'ata, kamar wacce k'walwarta ta samu matsala haka take fad'in "Ammar ka sake ni na tashi nayi sallah, bana son haka wallahi ko kad'an, wai kai kake da aljanna ne da zaka saka ni a ciki? Ko so kake Allah ya k'ona ni." Bai saketa ba bai kuma tashi ba saida Ummy ta shigo dubata saboda Hamna data fita tana kuka kuma ta k'i magana, da sauri ta fita ta d'auko allura ta zo ta mata, ba jimawa bacci ya d'auketa kad'ai ya sake ta. *Kullum* haka Amna take tunda ta haihu, mai saurin kuka da tausayi baya iya tsayawa kusanta saboda maganganunta masu karyar da zuciya ne, indai idonta biyu ba bacci take ba to maganganu ne zatayi ta sakowa, duk wanda zai zo ganinta saita mishi nasiha, ka kula da yaranka kn kana da su, ka kula da mijinka in kana da shi, ka dage wajen karatunka in mai karatu ne, hakan ne yasa duk wanda yaje ganinta sai dai ya dawo yana zubar da hawaye, a cikin k'ank'anin lokaci kowa maganarta yake. Yaro kam ko da ta haife shi dama aka d'orashi kan madara, da fari anyi hakane saboda ganin jikinta, amma yanzu abinda ya tabbatar ma kowa tana jin jiki shine, duk yanda yaron zaiyi kuka a kawo mata shi ta bashi nono saita k'i, haka zata dage ita ba zata bashi nono ba, sai manya suka fara tunanin ko iska ne dan babu abinda basa yi, addu'a aka dage da mata amma babu abinda ke sauyawa, wani lokacin tana bacci haka zaka ga hawaye na bin fuskarta, data farka sai dai ta tashi da kuka, to fa zata iya yin awa goma ba tace um bare um um ba, haka suka kwashi kwana *bakwai* a asibiti, sallamarta akayi suka koma gida dan sun ce ciwonta bana asibiti bane. *Ranar da* suka dawo gida... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _62_ *A ranar da* suka dawo gida kuma wani ikon Allah sai abun yayi sauk'i, ta ci abinci sosai tayi wanka ta gyara kanta sosai, kowa yayi farin ciki da faruwar hakan, musamman Hamna tafi kowa farin ciki, har yamma dai babu wata matsalar komai, yaro dai ne tana saka shi a nono zata cire shi ta aje, an idar da sallah magriba Ummy ta kalli Hamna tace "Hamna ki taimaka ki siyo mana kayan sanyin da za'a saka mishi mana, dan da alama garin akwai hadari." Amsawa tayi da "To Ummy." Mik'ewa Ummy tayi tana fad'in "Bari na d'auko miki kud'in." Da sauri tace "A'a Ummy ki barshi ma akwai a hannu na." Da sauri Amna dake zaune k'afafu mik'e ta d'aga rigarta inda aka mata aiki tace "Kin gani ko Ummy, zata kula dasu ko bayan ba raina." Hararanta Hamna tayi tace "Uwarki zan ci kika sake mana maganar mutuwa." Da sauri tasa hannu ta rufe baki tace "Nayi shiru to, yi hak'uri tafi Hajia." Murmushi Hamna tayi ta tashi ta fita, a farfajiyar ta had'u da Shureim da gudu ya tareta, dafa shi tayi tace "Daga ina kake?" Cikin muryarshi ta yara yace "K'ofar gida ni da yaya Ammar da Appa." Kallonshi kawai tayi da ido, wanda ya kamata ya kira Appa shi ya kira da yaya, wanda ke mazaunin kakanshi kuma ya kira da Appa, wannan wace irin *BADAK'ALA* ce? Cikin tunani bata san ta fara tafiya ba saida taji ya rik'e hannunta yana fad'in "Aunty ina zaki je? Ina zuwa." Kallonshi tayi tace "To muje mu siyowa sabon bebynmu kaya ko." Da gudu ya rigata k'arasawa wajen motar, bud'ewa tayi ta shigar dashi sannan ta shiga, mai gadi na bud'e mata k'ofar anan ta ganshi tsaye tare da Abba da Labaran, sauke gilashin tayi tare "Abba barkanku." "Ina zaki je?" Ita ce tambayar daya jefo mata, cikin ladabi tace "Ummy ce ta aike ni na siyowa bébé kayan sanyi, amma yanzu mun dawo dan tace akwai hadari a gari." Cikin sakin fuska yace "Shikenan sai kin dawo." Kallon Shureim yayi yace "Hein ba magana?" Ammar kawai ya kalla yace "Yaya na tafi." Murmushi ya masa yace "Saika dawo, ka kula da kanka." Wucewa tayi suka d'auki hanya, sun bar nan kenan Amie ta zo yin barka, gaishesu tayi suka amsa ta tambayi Ammar ya mai jiki da bébé, cikin amon muryar da yake nuna babu wasa ya amsa mata, ciki ta shiga kai tsaye b'angare Amna ta nufa, nan ta samu Ummy suka gaisa, saida suka gama gaisawa fa Amna sannan tace "Ummy ina Hamna take?" Cikin sakin fuska tace "Hamna ko bata jima da fita ba, amma yanzu zata dawo nasan ba zata kai ko kasuwa ba." Hira suka fara tab'awa da Amna sai Ummy data bar musu falon, ba jimawa da fitar Ummy kuma Hamna ta dawo, Zeituna ta ci karo da ita saita fad'a mata yanzu Ummy ta shiga ciki, dan haka saita shiga kawai inda Shureim ke mata rigimar ta koma yawo dashi, kai tsaye d'akinta suka shiga ta same ta tana duba wasu kaya, kallonta tayi tace "Har kun dawo wai?" "Wallahi Ummy, kinga kayan." Ta fad'a tana mik'a mata ledar, bud'ewa tayi tana dubawa sai Shureim dake kamo hannunta da k'arfi yana fad'in "Ki bani ni, ki bani." Umly ce ta kalleshi tace "Wai me za'a baka?" Dan kar Ummy ta dakeshi yasa Hamna sakar masa makullin, yana jin ta sake masa saiya fita a guje ta bishi da kallo, tana juyowa suka had'a da Ummy dake murmushi, cikin taushin murya tace "Ki k'ara hak'uri Hamna, insha Allahu komai ya kusa zuwa k'arshe, tunda a mahaifin yaron nan ya canza al'amuran gidan nake son fad'a ma Hajia, matsalar d'aya ita ce ta yanda zan fara fad'a, amma nasan ko da na fad'a rai ba zai b'ace ba kamar zamanin baya." Cike da damuwa Hamna ta kalleta tace "Ummy ni kaina tsoro nake ji, wallahi kullum tunanin al'amarin gigita k'walwata yake, duk da yanzu dai abubuwa sun canza, amma muyi kallon abun ta b'angaren yer uwata da kuma Abba, Ummy ya zasu ji idan suka ji maganar nan, ya yer uwata zata kalleni taji wai Shureim d'ana ne, d'an nawa ma wanda na haifa tare da mijinta, duk da dai kafin aurensu ne amma abun akwai gigitarwa, sannan Abba da yake mishi kallon d'an shi shima ya zaiji Ummy?" Jinjina kai Ummy tayi tace "Wallahi Hamna karki so ki tona raina kiji yanda a kowace rana nake bacci da fargaban nan, ni kaina nasan wannan abune mai matuk'ar d'aure ne, abune da ko da ya tab'a faruwa to ba dai a k'asar hausa ko kuma anan kusa ba, k'anwata Gaishata da bana b'oye ma komai, amma sai gashi wannan karan har alk'awarin fad'a mata da nayi bai cika ba, Hamna tun tana tambayata na fad'a mata har ta kai ta gaji ta daina, ni kaina bansan ta inda zan fara kawo k'arshen labarin nan da nine na fara shi ba tun farko." Cikin jimami tace "Kawai Ummy mu jira Amna ta samu lafiya a gama sabgar nan, kukan kura kawai zamuyi mu fad'a, in ya so ayita ta k'are kawai ko mun huta mu ma." Jinjina kai tayi tace "Allah ya shige mana gaba." Jin motsin zasu fito yasa *Amie* barin wurin da sauri wacce data mik'e zata tafi Zeituna ta fad'a mata ai Hamnar ta dawo tana wajen Ummy, tana zuwa yayi daidai da jin wannan babban sirri da ake ta b'oyo, da sauri ta koma b'angaren Amna ta zauna sai ga Hamna sun shigo, kallonsu take tana ta sak'a da warwara, sai dai ta girgiza kai kawai tayi murmushi, sai taji ma ta kasa tashi ta bar gidan, Amna da Hamna take kallo tana hasaso Ammar a idonta, lallai duk cikin lamarin Amna aka rainwa hankali, to miye abun b'oye mata ana zalintarta, kai ba zai yiwu ba wallahi, *gwara komai ya fito uban kowa yaji duk a k'one tare*, haka ta ci gaba da zama har k'arfe *09:00* dare yayi. Mutanen d'akin sun rage daga Amna da Hamna sai Amie, sai kuma Husseina wacce suke kwana tare amma tana nesa dasu sai gyangyad'i take, Hamna ce ta tashi ita ma tace "Besty bari na fad'awa Ummy saina aje ki gida." "Ok besty." Ta fad'a tana binta da kallon yar rainin hankali, saida ta ga fitarta ta gyara zama ta kalli Amna da kyau tace "Amna ke fa yanzu nan baki san komai ba ko?" Kallonta tayi tace "Komai kamar me fa?" Girgiza kai tayi tace "Allah sarki, gaskiya Amna ana cutarki a gidan nan, mijinki, yar uwarki da kuka fito ciki d'aya, da kuma Ummy, sun taru suna raina miki hankali." Duk mutanen da Amie ta ambata mutane ne da suka zama dunk'ulen rayuwarta, mutane ne masu matuk'ar mahimmanci a tattare da ita, dukansu zata iya sadaukar da rayuwarta akan su, dan haka a take taji wani haushinta da tsanarta sun dira a zuciyarta, sama da k'asa ta kalleta tace "Ni dai a sanin dana miki ban sanki da gulma da yarfe ba, bansan kuma yaushe kika koyesu ba?" Murya k'asa k'asa tace "Amna wallahi maganar gaskiya nale fad'a miki, idan ma baki yarda ba to ki tambayesu kiji." A kausashe tace "Na tambaye su me Amie? Wai dama gulma kika zo ba dubiya ba? To tashi ki fita." Tab'e baki tayi ta mik'e tsaye ta kalleta tace "Dama ko a yan biyu akwai baud'add'e, ke kam ba zaki tab'a gane irin cutar da ake miki ba, amma idan mijin naki ya shigo ki tambayeshi waya haifi Shureim? *Shi ko mahaifinshi*, inhar gaskiya zai fad'a zai ce miki shine, in kuma k'arya zai fad'a zai fad'a miki mahaifinshi ne." Juyawa tayi tana fad'in "Sai anjima." Zata fita Hamna ta shigo, juyawa tayi ita ma tace "Yawwa to yi sauri muje Hajia tace kar na jima." Cikin wata irin murya Amna tace "Dakata." Tsayawa sukayi suka juya suna kallonta, ba tare data tashi daga inda take ba ta kalli Hamna ido cikin ido babu yanayin wasa tace "Ki koma ciki babu inda zaki kaita." Da mamaki Hamna tace "Me yasa?" "Saboda munafuka ce." Ta fad'a kai tsaye, murmushi Hamna tayi a tunaninta jikin ne ya motsa tace "Kiyi hak'uri kinji yer uwa, ba jimawa zanyi ba yanzu zan dawo." Da k'arfi tace "Hamna babu inda zaki kaita, in kuma baki yarda ba to kuje ga hanyar nan." Kallon Amie Hamna tayi ta k'yabta mata ido alamar su mata wayo sai a zahiri da tace "Besty kawai ki tafi tunda yer uwata bata so ba zanje ba." Jinjina kai Amie tayi ta fita, Hamna na ganin haka ta kalli Amna tace "Akwai abinda kike so na miki ne ko ka naje na kwanta? Bacci nale ji sosai." Kallonta tayi tace "Kije ki kwanta saida safe." Juyawa tayi ta fita tana zuwa ta ja mota ta fita ta d'auki Amie, hak'uri ta bata kan abinda ya faru tace ba komai. Tana fita Amna ta bita da kallo, murmushi tayi tace "Ko yaushe Amie ta haukace kuma? Su yanzu nan mutane kallon mai hankali suke mata? Lallai ma Allah ya bata lafiya." Daga nan zaune ta saki wannan maganar kamar anyi rubutu a saman ruwa, jikinta ya bata Hamna ta tafi ta kai Amie gida ne, k'wafa tayi tace "Haba, kuje d'in mu gani." Saida sukayi nisa da gida kuma basu kai ko rabin gidansu Amie ba mota ta tsaya cak, ko da Hamna ta duba wajen dake bayyana idan mai ne babu taga tanki cike yake, nan ta shiga tayar wa amma mota shiru, tsayawa tayi tana girgiza kai tana murmushi a hankali take fad'in "Amna, Amna, amma zan ci uwarki, ni zaki wa iskanci." K'wafa tayi ta kalli Amie tace "K'awata, hak'uri zakiyi ki samu adaidaita ki hau, in dai ina tare dake to babu inda zan gusa." Da mamaki ta kalleta tace "Me yasa? Wani abun ne ya faru?" Murmushi ta mata tace "Ba zaki gane ba, kawai ki samu adaidaita." Bud'e motar tayi ta fita ta kalleta tace "To ke ya zakiyi?" Saida ta kalli titi tace "Karki damu, idan ma bata tashi ba zan kira a zo a d'auke ni." "Ok, ki kula da kanki." Jinjina kai tayi tace "Ok, saida safe." Nan ta samu adaidaita ta tafi, tun a hanya data shiga WhatsApp d'inta ta kasa hak'uri ta tab'o sauran k'awayenta su biyu, gulma ajali inji yan magana, haka suka jima suna tattaunawa suna fad'in ashe ta ma fisu iskanci, shine in taga suna rayuwarsu saita dinga nuna tana k'yamar abun, ashe ita har shege ma gare ta kuma da mijin yar uwarta. Saida ta ga tafiyar Amie ta kira Amna a waya, har ta kusa tsinkewa sannan ta d'auka tace "Lafiya? Har kin kaita d'in?" Dariya Hamna tayi dan su rabu lafiya kar ta jawa motarta kwana akan titi, cikin muryar rarrashi tace "Dan Allah yar k'anwata taimaka min ina so na koma gida kinji, dare kayi kar Abba ya min fad'a." Cikin kumburo baki Amna tace "Na k'i d'in, bani kika rainawa hankali ba?" Sake mak'ale murya tayi tace "Dan Allah fa nace." "To shinenan, ki bani hak'uri yanzu." Cewar Amna. Saida ta gyara murya tace "To aunty Amna kiyi hak'uri." Murmushi Amna tayi tace "Shikenan to kiyi sauri ki dawo gida kar wani ya sace min ke." Dariya tayi tana wa motar key tace "An gama zuciyata." Ko da ta kunna ta kama tana murmushi tayi baya baya ta d'auki hanyar komawa gida. *Da safe* Hamna na ta kai da kawon gyara falon an gama ma bébé wanka, duk inda tayi sai Amna tabi ta da kallo, tun bata lura ba har ta ankare, tun abun bai tsaya mata akai ba har ta fara tsarguwa da kallon, tsayawa tayi tana kallonta tace"Wai ke lafiya?" Sai kawai ta bushe da dariya kamar mahaukaciya, kallon mamaki Hamna ta bita dashi ta girgiza kai ta ci gaba da aikinta, Ummy na shigowa cikin shirin tafiya aiki da Shureim a hannunta, hannu ta tarawa Shureim tace "Zo nan." Takawa yayi ya je wurinta ya tsaya, rik'e hannunshi tayi tana mishi wani kallo kamar yau ta fara ganinshi, sai kawai ta matso dashi kusanta ta sumbaci goshinshi, saida ta d'auke bakinta ta sake kallon fuskarshi sai tace "Kai ni fa sai naji na fi sonka da aka ce yar uwata ma ta haifeka." Wani yamutsawar hanji Ummy da Hamna suka ji a lokaci d'aya, Husseina dake karin kumallo kallonta tayi irin kallon anya kuwa Amna, da sauri suka kalli juna suna zazzaro ido na alamar tambayar me ke faruwa, kallonsu Amna tayi a tare saida ta gama kallonsu sai tayi dariya ta nuna Hamna da hannu tace "Sakarya, ji yanda kika zaro ido kamar mahaukaciya, ko ke ma kin haukace irin na k'awarki?" Da sauri suka saisaita nutsuwarsu, sai Ummy data kalli Husseina tace "Anya Hajia kuwa lafiyarta k'alau?" Cikin murya k'asa k'asa tace "Ni ma dai abinda nake tunani kenan." Amna kam kallon Shureim ta sake yi tace "Baka tafi islamiyya ba kai?" A hankali yace "Yanzu Ummy zata kaini." Murmushi ta masa tace "Yawwa, kana ji ko? Ka dinga karatu sosai saboda ka zama babban malami, kana so ka zama kamar wannan kai ma?" Ta fad'a tana d'aukar wayarta, wa'azin *ustaz Rayyadun* (Allah k'ara girma malaminmu) ta nuna masa na vidéo tace "Ka gani ko? Ka zama kamar wannan kaima, kana so?" Kai kawai ya d'aga mata irin shi dai yana saurarenta, su dai kallonta suke har Ummy ta mik'e ta kama shi suka fita, hankalin Hamna ya kasa kwanciya duk a takure take jin kanta, ta k'i yarda su had'a ido da Amna wacce ita kuma take ta binta da kallo har yanzu, idan ta ga Hamna ta k'i kallonta sai ta bushe da dariya, duk wanda ya zo gidan haka zai iskota a wannan yanayin, gashi kuma Hamna babu damar da zata barta dan wani abun sai tace dole Hamna ce kawai zata mata, haka suka dinga wannan zama babu dad'i babu hira tsakaninsu, sai dai ita Amnar tayi ta nata maganganun masu kama dana mai shirin barin duniya. *Kwana uku* yau da faruwar wannan lamari, shirin biki ake ta yi sai dai ba wani da karsashi ake yinshi saboda yanayin jikin mai jego, kullum cikin taka tsantsan ake kan d'inkinta, ana yawan kwakwafarta kan rage magana da dariya mai k'arfi, amma abun sai a hankali in tayi wani abun kamar dai k'walwarta ce ta fara samun matsala. Yanzu ma Ammar ne ya shigo da babbar leda a hannu, ko da ya gaishe da mutanen d'akin ya nufi nashi d'akin, kamar daga sama aka tsinci muryar Amna tace "Ammar." Cak ya dakata ya juyo ya kalleta, *Ammar*? Tunda yake da ita daga k'uruciya har girmanta bai tab'a ji ta kama sunansa ba haka, dama dai waccen marar kunyar ce, su kansu mutane mamaki ne ya kama su jin yanda ta kira sunan nashi kamar sunan Ammar k'arami, shi kanshi Ammar k'arami saida ya juyo ya kalleta, har ya cire hannunshi daga abincin da yake ci zai taho tace "Ba kai ba zauna." K'ok'arin mik'ewa ta shiga yi hakan yasa Ummy taimaka mata ta tashi, saida taje kusanshi ta kalle shi tace "Muje ciki." Kallon Ummy yayi daga nesa, ita ma shi take kallo kallon nima bansan komai ba, wucewa yayi d'akin ta bishi a baya, sua shiga ta zauna kan gadonshi tana kallonshi tace "Kana ji ko? dan Allah ka kula min da yarana, ka dinga kaisu makaranta kan lokaci, kaji ko?" Shi mamakin yanda take masa magana kamar wacce ta haife shi ne ma yake, ganin bai ce komai ba yasa ta amso ledar hannunshi tana fad'in "Kawo to, watak'ila kallon nan da kake min dan ban karb'a bane." Aje ledar tayi kan gado ta mik'e zata fita sai kuma ta juyo ta kalleshi tace "Kasan wannan k'awar ta mu Amie?" Kai kawai ya jinjina mata yana ci gaba da kafeta da ido, dariya tayi sosai tace "Baka san ta hauka ce ba? Kasan haukan data zo min dashi gidan nan?" Kai ya girgiza mata kawai dan jin maganarta yake kawai a sama, wata dariyar ta sake yi tace "Wai a haukanta cewa tayi kai da Ummy da yer uwata kuna cin amanata, kasan me ta fad'a min?" Ajiyar zuciya ya sauke ba tare daya daina kallonta, jinjina kai tayi ta matso kusanshi cikin rad'a tace "Wai cewa tayi Shureim d'an ka ne, kaji fa mahaukaciyar, ta manta Ummy ce ta haife shi, to kuma ni ko wa ma ya haife shi ina son shi, inda yer uwar ta wa ta haife shi wallahi da naji dad'i." Kallon fuskarshi tayi da kyau sai tayi dariya tace "Kai ma ka girgiza ko? Karka damu ci gaba da abinda kake." Ko da ta fad'a ta juya a hankali ta bar d'akin, shi fa tunda ta fad'i haka gabanshi ya yanke ya fad'i, kawai bata aje hankalinta bane data fahimci tashin hankalin daya shiga jin wannan magana, ita dai ta d'auki abun wasa da k'arya da kuma hauka, amma shi baya da dalilin da zai k'aryata Amie, hasalima zai iya cewa ya yarda da abinda ta fad'a d'in, yana da gamsassun dalilai da hujojji. Yanda ya zazzare ido haka ya zauna bakin gado, tunani ya durmiya yana tuna faruwar komai sala sala, tabbas bayan faruwar al'amarin ne cikin Ummy ya bayyana, lokacin daya ga canji a jikin Hamna har ya so fallasawa Ummy ta jijjiga sosai har ta mare shi, sannan ta matsa sosai har saida aka mata hanyar data shiga sahun masu tafiya France kuma ta k'ara kan lokacin daya kamata ta dawo, kuma ai Hamna bata nan a lokacin, to kenan taya haka ya faru? Girgiza kai ya shiga yi yana ta tunanin abubuwa da dama, ji da yayi kamar kanshi zaiyi bindiga yasa shi mik'ewa da sauri ya fito. Har tsakiyar mutanen da take zauna ya ja hannunta inda hankalin kowa ya koma kansu, janta kawai yake ita kuma tambayarshi take ina zai kaita lafiya? Saida ya kaita kusan d'akin mai gadi ya tsaya ya saki hannunta, rik'e k'ugu yayi da duka hannayenshi yana kallon fuskarta kamar ba gobe, ajiyar zuciya ya sauke mai k'arfin gaske. Cikin wata sanyayyar murya amma sautin ta zai nuna maka babu wasa a cikinta kuma mamallakin muryar zai iya yin komai a yanzun yace "... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _63_ "Ummy, da gaske wai Shureim d'ana ne?" A firgice ta kalleshi yayin da taji har ruwan jikinta na neman tsayawa, yanda ta zaro ido zai nuna maka bata da gaskiya, gudun kar ya fahimta sai tayi saurin b'atar da firgicin ta jawo mamaki ta dasa a fuskarta tace "Ammar, wace irin magana ce wannan? Wane Shureim d'in?" Da hannu ya mata alamar ya isa haka tare da cewa "Ummy, kin sani na sani abinda ya faru, idan zan iya kawo miki hujojji na sai mu kwana anan ban gama ba, tun waccen lokacin ma nayi shiru ne saboda gudun b'acin ranki, Dan Allah Ummy inhar gaskiya ne abinda naji ki fad'a min." Cikin fad'a tace "Ammar wace maganar banza ce wannan? Ya zaka tasa ni a gaba kana tambayata wai Shureim d'anka ne? Zargina kake da cin amanar mahaifinka ko me? Ni sam ban ma fahimci me kake nufi ba." Matsawa yayi daf da ita murya k'asa k'asa yace "Ummy ba haka nake nufi ba, Shureim an ce d'ana ne dana haifa tare da Hamna, shine nake so naji gaskiyar." Cikin b'acin rai da d'aga murya ta rintse ido tace "Ammar bana son maganar banza, uwarka ce ya zaka sani gaba kana min wannan tambayar rashin mutumcin? Fad'a min wane d'an iskan ne yake son shiga tsakani na da kai da har ya fad'a maka wannan banzan shirmen?" Cikin fitar hayyaci da b'acin rai da yanayin da shi kanshi baisan yayi magana dashi ba ya d'aga murya sama da ta ta yana fad'in "Ummy babu wani dake son shiga tsakani na dake, magana ce ta fito kuma ina so na sani nima, a matsayi na na d'anki ina da hakk'in da zan san haka." Saida ya dasa aya ya iya jiyo sautin muryarsa can sama, dafe kanshi yayi da hannu biyu yana d'an murzashi a hankali, kallonta yayi ya rik'o hannayenta duka buyu yasa idonshi cikin nata yayin da take mishi kallon mamaki yace "Ummy ki daure ki fad'a min mana, da gaske d'ana ne ko kuma k'arya aka fad'a?" Cikin zubo da hawayen da suke nuna ta k'are min ta kafe shi da ido tace "Ammar waya fad'a maka maganar nan? Wane d'an banzan ne?" Kamar zai fashe d a kula yace "Ummy abinda nake so naji daban, abinda ke ma kike so kiji daban, amsar tana da sauk'i fa Ummy idan kikayi niyyar fad'a min, kawai zaki ce min eh ne ko kuma a'a." K'yabta ido tayi tana kallon gefenshi, jinjina kai yayi yace "Zan tabbatarwa kaina." Ko da ya fad'a ya wuce da k'arfi ya tunkari falon Hajia, da gudu gudu ta bi bayanshi tana fad'in "Ammar ina zaka je? Me kake shirin yi ne wai? Ammar..." Bai tsaya ba har saida ya shige falon, shigarsu yayi daidai da fitowar Hajia daga d'akin tare da duk yan kuci-kucin yaran suna ta mata shirme, da sauri ya tunkareta inda ya ga Shureim, hannunshi ya kama ya juya zai fita dashi Ummy ta rik'e hannun Shureim ita ma, juyowa yayi yace "Ummy dan Allah sake shi." Matsowa tayi kusanshi tace "Ammar baka da hankali ne wai? So kake ka min terere cikin mutane? Ina zaka kai shi?" Gyara tsayuwa yayi yace "Asibiti zamu je." Ko da taji yace asibiti tasan me zaiyi acan, sunkuyar da kai tayi k'asa sai Hajia data matso kusansu tana kallon kowane tace "Ku kuma lafiya? Meya faru ne haka?" Kallon Hajia yayi yace "Hajia, Shureimmm..." Yanda Ummy tayi saurin rufe masa baki yasa shi jan k'arshen sunan, kallonta Hajia tayi ta fahimci bata so taji, sai kawai ta kama hannun Ummyn da Ammar ta tura su d'akinta, Shureim ta kama hannunshi shima suka shiga ta mayar da k'ofar ta rufe, zaune tayi kan gado ta kallesu ta nuna musu kujerar dake d'akin mai kama data gwal tace "Ku zauna dan Allah." Ummy na kallon Ammar ta tsoma mazaunanta kamar tace wayyo ita wayyo kanta, a nutse ta kallesu ta tattara hankalinta gaba d'aya kansu tace "Me yake faruwa Sa'ada?" Cikin in'ina tace "Hha.jia, ba kommai..hajia." Murmushi tayi ta kalli Ammar tace "Ammar lafiya? Me yake faruwa da kake d'aga murya fiye data mahaifiyarka?" Ummy ya kalla ya sunkuyar da kai yace "Kiyi hak'uri Ummy ki yafe min, wallahi bansan na d'aga murya fiye da taki ba, kiyi hak'uri dan Allah." Dan motsa kanta tayi wanda yake nuna tace ba komai, Hajia ya kalla yace "Hajia, in baki manta ba na fad'a miki abinda ya faru tsakani na da Hamna shekaru kusan biyar kenan." Sororo Ummy ta kalle shi da wani fitinannan mamaki, ya fad'a mata? Yaushe akayi haka bata sani ba? Kuma shine Hajia bata nuna mata ta sani ba? Tana kallon bakinshi taji yace "Shine yanzu aka fad'a min Shureim d'ana ne, Hamna ce ta haife shi, kuma ina tambayar Ummy amma ta k'i fad'a min, Hajia ina so na sani d'ana ne ko kuwa." Hajia ma mamaki ne ya bayyana a fuskarta, kallon Ummy take tace "Sa'ada." D'ago kai tayi ta kalleta, d'orawa tayi da "Da gaske ne abind yake fad'a?" Cikin sanyin jiki tayi shiru ta kasa cewa komai, ba zata yarda ta sake yin k'arya ba, tunda gashi wacce tati shekaru ma yau ta fito, sai dai kuma ba zata iya amsa kai tsaye da eh ba, ganin wannan shirun na ta yasa Ammar kallonta da mamaki yace "Ummy me yasa kika yi haka?" Kallonshi tayi saita sake yin k'asa da kanta ta fara zubar da hawaye, girgiza kai yayi kamar zai yi kukan shima na tausayin mahaifiyarshi yace "Ummy me yasa kika aikata haka? Dama har soyayyar da kike min ta kai wannan matakin?" Fashewa ta sake yi da kuka sai kawai yace "Ummy in kinyi hakane saboda ki kare mutumci na dana Hamna, ai da fad'a min kikayi saina tayaki kare wa har zuwa lokacin da kike so kowa ya ji, idan kuma kinyi ne saboda gudun abun kunya da kallon da mutane zasu mana, Ummy ai naga ba akai na aka fara abun kunya ba, a gidan nan bani ne farkon daya fara aikata irin wannan laifin ba, Ummy ina kika kai tonton Labaran? naga shima ba da aure aka same shi ba kuma yana rayuwarshi hankali kwance, hasalima ba tare daya tab'a ganin mahaifinshi ya taka wani babban matsayi na rayuwa." Cikin nuna mata da hannu ya ci gaba da fad'in "Sannan ki dubi Huda, gata nan tana rayuwa cikin dangin mahaifinta ba tare da tsangwamar kowa ba, haka ma Junaid, rayuwarsa yake yi bai damu ba, kuma babu wanda yake iya d'aga ido ya kalleshi ya fad'a masa hanyar da aka same shi, Ummy sai ni ne dan na aje d'an gaba da fatiya za'a min zund'e da kinibibi, Ummy hakan ma ai tayar da lissafi ne yayi, kinga kenan zai zamana a kowane d'aki akwai shege." Yanda ya fad'a da k'arfi yasa ta rintse ido, kallon Hajia yayi yace "Hajia, ki fad'a mata ko ta kwantar da hankalinta ta nuna wa yaro ubansa, ki fad'a mata abun kamar a jininmu yake." Wani murmushin rainin hankali Hajia tayi ta kalli Ummy tace "Hakane Sa'ada, ki fad'a masa in dai har kinsan d'ansa, karki ji komai a game dani, kamar yanda ya fad'a ne a kowane d'aki akwai yaro irin Shureim, sannan ni kaina da kike gani fa sanda nake budurwa na tab'a yin cikin nan, ni na ma fisu laifi saboda zubarwa nayi, su kuma basu zubar ba sun haifi abinsu, to kika sani ko fantin dana shafawa kaina ne har yanzu yake biyar zuri'ata." K'ara saita muryarta tayi ta dafa hannun Ummy tana kallon fuskarta tace "Sa'ada, ba zan manta sanda aka kawoki gidan nan ba, ni shaida ce Hassan ya same ki a tsarkake, haka ma Hadiza ina d'aya daga cikin wanda suka taimaka mata a daren farkonta, wannan duk ya isa ya zama hujjar da yaranku zasu k'auracewa zina, amma inda gizo ke sak'ar shine ni, ni d'in ne duk ni na gurb'ata muku iyali, ki dubi Alhaji bawan Allah wanda bai san hawa ba bare sauka, shi ya kamata ace yafi kowa damuwa, amma shi ma ido ya saka min yayi hak'uri dani har saida mai rabawa ta raba." Numfasawa tayi tana ci gaba da kallonta tace "Sa'ada, ki dubi girman Allah ki fad'a masa gaskiya, Shureim d'an waye a cikin Ammar da Hassan?" Kutumar bala'i! Shine abinda Ummy ta fad'a a ranta, Hajia! Ciki? Lallai ma, idan ta fahimci inda zancen ya dosa duk ita ce ma silar komai, lallai su Hajia manya, k'warin gwiwa ta samu daga jin kalaman Hajia, sai kawai taji bari ta fad'a da alama ta samu sauk'i. Ba tare data kallesu ba ta fara goge k'walla cikin muryar data sha kuka tace "Gaskiya ne, Hamna ce ta haife shi bani ba." Hajia ce tace "Amma Sa'ada taya kika iya shirya lamarin nan ba tare da mijinki ma ya sani ba?" Tsaf Ummy ta fad'a musu duk yanda akayi har haihuwarta, d'orawa tayi da "Wallahi a lokacin na tsorata ne sosai na rasa yanda zanyi, tunanin hukuncin da zaku d'auka akan shi ke da mahaifinshi ya k'ara tunzari muka ci gaba da b'oye, amma dan Allah kuyi hak'uri ku yafe min, ya lalata rayuwar yarinya ni kuma na taimaka masa, a idon doka da mutane duk mun aikata laifi." Cikin kuka sosai tace "Na sani da ace wani daga waje na ya ci zarafinta, wallahi sai inda k'arfina ya k'are wajen bi mata hakk'inta, da nayi anfani da mahukuntan dake gidan nan da kud'i da muk'amin mahaifinta wajen ganin na kai ko d'an uban waye k'asa, amma daya zama d'ana ne saina kasa yin komai na lullub'eta tare da laifin ina ta hura mata wuta, banda fargaba idan aurenta ya tashi, na yarda da kaina da gyaran dana koya iyaye da kakanni, dole zata banbanta tsakaninta da budurwa, shiyasa kullum fatana Allah ya fito mata da miji tayi aure." Kallonta duka suke sai kuma ya juya ya kalli Shureim dake tsaye gaban madubin Hajia yana kallon kwalaben turaren da suka d'auki hankalinshi saboda kyawunsu, kamo hannayenta yayi ya rumgume cikin muryar alhini yace "Yanzu Ummy wannan dalilin ne yasa kike ta nesanta ni dashi dama? Shiyasa ba kya so kiga muna kusantar juna sai kin raba mu?" Kallonshi tayi tace "Kayi hak'uri Ammar, nasan yanda soyayyar jini d'aya take, duk yanda zan nisanta ku a cikin dubu zaku iya gane junanku, kawai dai ina nesanta ku ne bana son kuyi saurin gane junanku." Sakin yaron yayi ya rumgumeta kamar zaiyi kuka yana fad'in "A da tunani na shine baki sona, idan kina hantarata da zagi na sai naga kamar baki damu dani bane, amma yau na gane babu wanda kike so sama dani Ummy, duk wannan kasadar saboda ni ne kika d'auketa, nagode Ummy, dan Allah ki yafe min komai dana mike." K'ulli ta sakar mishi a baya tana fad'in "Shashashan banza, taya wai zaka ce bana son ka bayan a cikina na haife ka." D'ago kai yayi yace "Hauka na ne ke nuna min haka Ummy." Rank'washin shi tayi a kai tana murmushi tace "Kai fa na daban ne yarona, tashin hankalin da ka so min yanzu shine nayi gudu tun tuni yasa ban fad'a maka ba, nasan in ka sani zaka shelanta ne kowa yaji." Dariya yayi yana sosa inda ta rank'washeshi yace "Kamar kin sani kuwa Ummy." Wani kallo ta masa tace "Au! Kamar ma na sani ne? Wa ya fini saninka a duniyar nan." Hajia dake dariya tana kallonsu ne tace "To ku bani hankalinku nan." Juyawa sukayi suka kalleta cikin nutsuwa, saida ta kallesu tace "Maganar nan ba zata tsaya iya nan ba, dole akwai wad'anda zamu fad'a ma su san halin da ake ciki." Kallon juna sukayi suka sake kallon a tare da mamaki Ummy tace "Hajia su wa kenan?" Cikin kallon basira tace "Hassan, dole ya sani ko da bama so, da kuma Husseina wacce yanzu ni kaina nake girmamata, ita kwatankwacin Alhaji ce da baya nan a gidan nan, dan haka ita ma zata sani, sai kuma Amna amma bansan ku me zakuyi tunani a game da ita ba?" Tashin hankalin Ummy da ma Hajia ce kuma gashi ta tsallake cikin sauk'i, dan haka yanzu ita bata damu ba duk wanda ma zai ji ya ji a shirye take, cikin ladabi tace "To Hajia ke me kike gani?" Saida ta gyara zama tace "A gani na ni dai a fad'a mata, ba dan komai ba sai dan halin rayuwa." Da sauri Ammar yace "A'a Hajia, kar a fad'a mata gaskiya ina jin tsoro." A tare suka kalleshi da mamaki, Ummy ce tace "Tsoro? Ammar kai d'in? Lallai." Hajia ce tayi murmushi tace "Ashe dai har abun ya zo inji me tsoron wanka, Ammar kai ne baka so a fad'i gaskiya, har kake cewa kana jin tsoro, tsoron ma matar aurenka." Kallonta yayi yace "Hajia ko yanzu wallahi a shirye nake dana fad'awa duk duniya waye Shureim, ita dai ce kawai bana son ta sani." "Saboda me to?" Cewar Ummy tana kallonshi. Saida ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "Saboda tana d'aya daga cikin mata ukun dake kassara tunani na, tana d'aya daga cikin wanda tunanin al'amarinsu ma kad'ai yake firgita min nutsuwa ta, tana d'aya daga cikin sanyin idanu na, d'aya ce daga cikin ukun da bana son ganin tashin hankalinsu." Kallon Ummy yayi yace "Taya zan so nutsuwarta ta bar gangar jikinta kan abinda na aikata, kwanciyar hankali na ce ita, taya zan so taji abinda nake da tabbacin zai gusar da hankalinta, idan kuma haka ta faru ni wa zai nemo min nawa hankalin, mallakina ce kuma babban rabon dana gada a gidan duniyar nan, idan zan misaltata da gona to bansan adadin girman ekar dake cikinta ba, daga ni har yarana ita ce duniyar mu." Ummy da taji hawaye sun cika idonta ne tace "Bansan ya zata ji idan aka fad'a mata ba?" Murmushi yayi yace "Ummy kunsan a ina naji kuwa?" Girgiza kai tayi tana kallonshi har ya d'ora da "Ita ce ta fad'a min." Hajia ce tayi saurin cewa "Ita wa?" "Amna mana." Ya fad'a yana kallonta, zaro ido duka sukayi sai kuma Ummy tace "Amna? To ita a ina taji? Amma kuma banji tashin hankali ba?" Murmushi ya sake yi yace "Ummy yarinyar nan tayi a rayuwa wallahi, ita ta fad'a min da kanta, amma abun tsoratarwa ta d'auki abun kamar tatsuniya, abun ma dariya yake bata sabodaa ganinta abu ne da ba zai tab'a faruwa ba, sannan tana da yarda akai na da kuma yar uwarta d'ari bisa d'ari." Da mamaki tace "Amma a ina Amna taji maganar nan?" Ammar ne yace "A wurin Amie k'awarsu." Da wani mamakin tace "Amie kuma? A ina Amie taji to? Babu fa wanda yasan da maganar nan." D'aga kafad'a yayi irin ohon nan yace "Ki tambayi *uwar Shureim*." Wani galala Ummy ta kalleshi a ranta tace "Kaji wani wai uwar Shureim, to wannan ya ma bari har a gama fad'a ma wanda ya dacen kafin ya fara kiranta da wannan sunan?" A fili kuma cewa tayi "A gaskiya bana tunanin zata fad'a mata, amma kuma abun da mamaki sosai." Bud'ar bakinshi cewa yayi "Ummy karki ba kanki wahala wajen sanin yanda akayi taji, kawai share zancen." Hajia ce tace "Kunga, hak'uri zamuyi mu daure a fad'a mata, kamar yanda na fad'a muku ko saboda halin rayuwa, abinda nake so ku fahimta shine idan yanzu bata sani ba a k'arshe kuma ta ji a wani wurin aka tabbatar mata da gaskiya, to fa ba zata ji dad'i ba kuma mummunan abunda ba ayi tsammaninshi ba zai iya faruwa." Jinjina kai yayi yace "Gaskiya ne, na yarda a fad'a mata amma ba yanzu ba gaskiya." Ummy ce tace "Eh gaskiya kam, bai kamata ba dama a fad'a mata yanzu, saboda har yanzu ni dai jikin nan naya yana bani tsoro." Hajia ce tace "Shikenan yanda kuka ce, a jira ta samu lafiya sai a sanar da ita." Ammar ne ya mik'e tsaye ya kama hannun Shureim yace "Zan fita mu dawo." Da murmushi Ummy tace "A dawo lafiya." Da kallo suka bisu har suka fice, Ummy ma godiya ta ma Hajia ta fita tana jin kamar ta taka rawa tsabar farin cikin da take ciki. Wani ikon Allah suna fita farfajiyar zasuyi wajen ajiyar motoci suka had'e da ita ta dawo daga wajen kitso, cikin murna ta bud'e hannayenta zata d'auki Shureim, baya yayi da shi yana kallon fuskarta, kallonshi tayi fuska a had'e tace "Shureim zo nan." Wani murmushi ya mata, bayan tsawon lokaci rabon da bakinsu ya had'u yau sai gashi dalilin Shureim yace mata "Fita zamuyi." Bata kula da abinda ya fad'a mata ba ta zura hannu zata jawo shi, k'ara baya yayi dashi yana kallonta shi ma fuska a had'e yace "Na ce fita zamuyi dashi yanzu, ko kuma ban isa bane?" Wani kallon rashin mutumci ta masa tace "To miye na tambaya ta bayan gashi ka bawa kanka amsa." Kai tsaye take nufin bai isa ba kenan, matsowa yayi kusanta sosai har numfashinsu ya fara gauraya ya kalli k'wayar idonta kamar yanda take kallon na shi babu rusunawa yace "Wallahi *kinci albarkacin yaron nan dake tskaninmu*, ba dan haka ba da saina na zubar miki da k'ananan aljanunki, marar kunya kawai da baki iya girmama mutane ba." Zaro idon da tayi alamar ya akayi haka yasa shi saurin katse mata lissafi da cewa "Eh, na sani, sai kuma yaya yanzu? Shashasha kawai." Wucewa yayi har ya fara tafiya sai kuma ya tsaya ya juyo, duk da bata juyo ba saida yayi murmushi yace "Zaki iya tuna na tab'a fad'a miki sau d'aya nake aika d'an sak'o na kuma ya isa inda nake da muradin yaje? Ki kama kanki yarinya ko kuma..." Wucewa yayi rik'e da hannun Shureim ya barta tsaye, saida taji sun tayar da mota tayi saurin wucewa ciki kamar zata tashi sama, bata kula ba tayi karo da Ummy dake niyyar zuwa b'angaren Amna, suna had'a ido ta kama hannunta da k'arfi ta jawota suka k'arasa fitowa daga falon, saida ta juya ta ga babu kowa tace "Ummy, waya sanar dashi maganar nan?" Dariya Ummy tayi ganin tsoron dake fuskarta duk ta furgice tace "Kwantar da hankalinki to? Ni ai ke zan tambaya wa kika fad'awa har ya fad'a ma Amie maganar nan?" "Me? Amie kuma?" Cikin mamaki tace "Ummy ni ban tab'a maganar nan da kowa ba." "To ya akayi Amie taji har ta fad'awa Amna?" Gaba d'aya idonta ta k'walalo waje ta dafe k'irjinta dake bugawa da k'arfi, dafata Ummy tayi tace "Kwantar da hankalinki mana." Girgiza kai tayi tace "Ummy Amna fa kika ce? Taji wannan maganar? Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Ummy na shiga uku na lalace, Amna da shegiyar zuciya." Murmushi ta mata tace "Yanzu dai ki fara nutsuwa tukuna sai kiji abinda ya faru." Cikin saurin maganar da bata san ta iya shi ba tace "Ummy ina maganar nutsuwa kuma kawai ki fad'a min komai." A hankali Ummy tace "Shi ya fara samu na da maganar yace Amna ce ta fad'a masa, ita ma kuma wai Amie ce ta fad'a mata, amma fa ita ta d'auki maganar da wasa, muna cikin maganar kuma Hajia ta fahimci akwai matsala ta ja mu d'akinta." Shirun da tayi ya ba Hamna damar d'ora hannayenta saman kanta tace "Na shiga ni Hamna, na mutu shikenan, Ummy sai me ya faru?" D'orawa tayi da "Magana mukayi ta fahimtar juna, Hamna idan kika ga yanda Hajia ta fahimce ni har ta bamu shawara wallahi zakiyi mamaki." Da sauri ta rik'o hannayenta tana fad'in "Ummy kina nufin ba tayi fad'a ba?" Girgiza kai tayi tace "Ko kad'an in fad'a miki." Kamar zata fashe da kuka tace "Amma kuma Ummy Amna fa? Ina tsoron ranar da zata ji da abinda zata iya yi wallahi." Cikin taushin murya tace "Insha Allah ita ma zata fahimce mu fiye ma da Hajia, abinda kike tunanin tayi ba zai tab'a faruwa ba, Amna tana da hak'uri sosai." "Amma kuma tana da zuciya Ummy." Ta fad'a tana sako siraran hawaye, hannu tasa ta shafe mata tace "Dan Allah karki d'aga hankalinki Hamna, ki nutsu ki shiga ki samu kiyi wanka ki ci abinci, karki yarda wani ya gane kina cikin damuwa, muyi addu'a yanzu Allah ya bata lafiya, ke baki ji abinda ta fad'a ba kwana uku da suka wuce, kallon mahaukaciya ma take wa Amie fa." Jinjina kai tayi tace "Shikenan Ummy." Shigewa tayi ciki Ummy ma ta nufi b'angaren Amna. Ko da taje ta samu an ba wa Amna maganin zazzab'i tasha, d'aki suka ce taje ta kwanta ta huta da kwaramniyar nan, da shigarta d'aki baifi minti sha biyar ba Hamna ta shiga dubata, kwance ta same sai rawar d'ari take, ko da ta tab'a jikinta taji zafi sosai kamar garwashin wuta, idonta sunyi jawur da su kamar ba nata ba, Ummy ta fito ta fad'a ma suka shiga tare, ko da ta ga jikinta tace kawai su kaita asibiti, ba b'ata lokaci Hamna ta jasu dan Ammar ya riga da yayi nesa da gida, acan ya samesu har san jona mata k'arin ruwa. Tsananin zafin jikin baya raguwa sai sama yake, cikin d'an lokaci k'ank'ani ta canza ta fice a hayyacinta, da fari an k'ara mata ruwa sai aka nemi jini ma aka k'ara mata. Allah da ikonsa kafin gari ya waye ba zaka tab'a kallon Amna kace ita ce ba, ta gigice ta canza duk ta disashe ta zama abar tausayi, gashi tayi kamar ta kumbura a jikinta, zuwa wayewar gari saida aka saka mata wani tiyo dake kai mata ruwa, a hannayenta k'arin ruwa da jini, n'aurar taimaka mata wajen numfashi abubuwan kamar ba a jikin mutum ba. *Sai daren ranar* kad'ai likitoci suka d'an samu kan matsalar, Ammar ne zaune gaban likitan ya k'ura masa ido inda zuciyarsa ke dukan uku uku, ya kasa had'a yawu ko alama sai tattarasu yake yana son turasu mak'ogoronshi amma sun k'i wucewa, likitan ne ya mayar da hankalinshi kanshi cikin nutsuwa yace "Docteur ya kukayi sakaci haka da marar lafiya? abu ne dake matuk'ar wuya samun irin haka a lokaci d'aya, kuma da an ankara da wuri da an cire mata d'aya a barta da d'ayar, yanzu gashi lokaci ya k'ure mana sosai." Ammar dake kallon bakinshi kamar kurman dake fahimtar yaren leb'e ne yace "Ban cika fahimtar ka ba fa, ka min gwari gwari zan fahimta." Saida ya dan furzar da iska ya kalli tsakiyar idonshi yace "Duka sun lalace, k'wadarta." Da sauri ya dafe kanshi da hannu biyu, sosai yake matse kanshi yana so yaji ya daina sara masa amma abun ya ci tura, da k'yar ya d'aga kai ya kalle shi yace "Ta yaya? Duka biyun zasu lalace lokaci d'aya? Ta yaya dan Allah? Me ye abunyi yanzu?" Cikin rashin karsashi yace "Mu kan mu abun ya bamu mamaki, dan abune da bai cika faruwa ba gaskiya..." Katseshi yayi da cewa "Me ye abunyi yanzu?" Cikin girgiza kai yace "A gaskiya yanayin jikinta ma ba zai bayar da damar da za'a fara mata dialyse ba, dan kaga tana jin jiki sosai kuma kowane dialyse zatayi perdre d'in 10 kg, dan haka ina ga mu..." Da k'arfi ya mik'e tsaye yana fad'in "Dan haka ayi me? A barta ta mutu kenan? Haka kake so ka ce?" Girgiza kai yayi yace "Non docteur, amm..." Cikin daka masa tsawa yace "Kaga fad'a min mafita kawai, ina so ka fad'a min abinda zanyi matata ta samu lafiya, bana son ganinta a halin da take cikin nan." Shi dai yana so su rabu lafiya dashi sai kawai ya rubuta masa magaunguna yace ya siyo, da gudu ya fita kamar wanda yasha giya dan har yanzu kanshi mugun sara masa yake. *Kwanansu* biyu a asibiti, abubuwa sun k'ara dagulewa, tun safiyar yau da Ammar ya shigo d'akin ta fara masa nasiha ya rage zuciya ya dinga hak'uri ya kula da yara waye waye, sai kawai zuciyarsa ta karye ya fita daga d'akin, Allah ya sani har zuciyarshi yana son Amna kuma yana son zama da ita, amma baisan wacce k'addara ce ke shirin raba shi da ita ba, baisan ilimin dake cikin rashin lafiyarta ba, tunda ya fita ya zauna cikin masallacin asibitin bai sake tashi daga nan ba, yanda ya ga safiya a cikin shi haka ya riski rana da dare. Al'amarin bai sake tashin hankalin kowa ba saida ta nemi a kawo mata yaranta, daga kwance haka take shafar kawunansu tana musu murmushi, Ameera da tafi kowanensu shak'uwa da ita ce ta kwanta kan jikinta tana kuka, Ameer ne ya jayeta daga jikinta yana fad'in "Ke baki gani bata da lafiya." Fizge hannunta tayi ta sake kwantawa kan jikinta, Ummy dake tsaye kusansu ne ta kalli Hamna dake tsaye ita ta kawosu tana hawaye, hannun Ameera ta kama cikin muryar kuka tace "Beby na zo mu je ko? Zaki sha ice cream?" Mak'ale kafad'a tayi tace "Um um." Saida ta share hawayenta ta sake kamota tace "Muje kinji har da madara zan siya miki." Duk da bata saki jikinta ba haka ta bi Hamna zasu fita, cikin muryar da bata fito sosai ba Amna tacej "Yer uwa." Juyowa tayi tana kallonta ta tako a hankali ta zo ta tsaya, hannu ta mik'a mata ita ma ta zuro mata na ta hannun ta rik'e gam, murmushi ta saki mai kyawun gaske tace "Karki manta dani kinji, ki ci gaba da min addu'a, ke da yah Ammar zaku kula min da yarana, nasan da haka ban da matsala, karki rabu dasu duk wuya, yah Ammar zai shiga damuwar rashi na, ki...kkk...kw..." Ganin ta kasa fad'ar kalmar kuma ita kuka ya ci k'arfinta yasa ta fizge hannunta da k'arfi ta tashi a guje ta fita, bata tsaya ba saida ta kai k'ofar asibitin ta durk'ushe nan tana kuka da iya k'arfinta. Ko da ta fita Amna ta kalli inda Hajia take ta mata alamar ta zo, matsowa Hajia tayi tana kuka ta rik'e hannunta tace "Amna dan Allah kiyi ta addu'a, insha Allahu zaki tashi kinji." Sakin hannun Hajia tayi ta kalli inda Hadiza ke tsaye wacce ta zo da taji jikin ya k'i kyau, ita ma alamar ta zo ta mata ta rik'e hannunta, magana take yi amma bata jin komai, a hankali ta durk'usa ta kai kunnenta kusan bakinta, cikin sanyin muryar da bata fita tace "Mama, ki yafe min, ki yafe min, Abba ma ya yafe min, yah Ammar, ki kira min yah Ammar na rok'i gafararshi, dan Allah ki ce masa ya zo ina son ganinshi, Mama, Mama, Mama, sau uku na kira sunanki ko? Dan Allah ki ce Hamna ta zauna tare da yah Ammar da kuma yara na, zata iya kula dasu kamar yanda nake yi, dan Allah Mama, kinji, kinji ko." D'agowa tayi tace "Na ji Amna, kiyi ta kalmar shahada a bakinki, bari na kira miki Ammar d'in." Tashi tayi da sauri ta fita, amma tana fitowa ita ma ta tsaya cikin wani d'aki da babu kowa ta shiga rera kuka, ta d'auki kusan minti ashirin tana kuka kafin ta fita ta same shi zaune ya had'a kai da gwiwa, da sauri tace "Ammar, ka zo dan Allah Amna tana son ganinka." Tasowa yayi daga cikin masallacin ya matso kusanta cikin layi na galabaita yace "Mama dan Allah ku rabu da ita, zafin ciwo ne ke damunta kawai." "A'a Ammar, ka zo kawai tunda tace tana buk'atar ganinka." Cike da kasala yace "Shikenan muje." Juyawa tayi ya saka takalminsa ya bi bayanta, ji yake gabanshi na tsananta fad'uwa, ko da suka isa d'akin suka ji ana ta kalmar shahada da kabbara, babbar kalmar data daki zuciyarsa ita ce ta"Allah yasa anyi sa'ar tafiya." Suna shiga tare suka ganta ruf, da d'aya d'aya ya shiga kallon mutanen d'akin, yanayin kowa da furucin bakunansu ya tabbatar masa da abinda zuciyarsa ke raya masa, wani tartsatsi yaji daga kanshi har zuwa k'afarshi, kamar wani ne ya turashi sai ganinshi sukayi ya fad'i warwasss... *Alhamdulillah* 14/10/2020 à 00:58 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _64_ Da sauri Ummy tayi kanshi ta durk'usa tana duba shi, mik'ewa tayi da sauri zata fita daga d'akin saiga Amar da Jibril sun shigo da sallama, da sauri ta kallesu tace "Yawwa ku kama shi dan Allah, ina zuwa." Fita tayi daga d'akins su kuma suka tallabe shi suka fito dashi, a wani d'akin aka kwantar da shi Ummy duk ta rikice sai wasu likitocin ne suka diba shi suka saka masa ruwa. *Allah mai girma*, jinjiga, girgiza, d'imuwa da zautuwa babu wanda baiyi ba, Amna dai ta tafi gidanta na gaskiya cikin sa'a, duk wanda ke d'akin a lokacin ya shida tayi kalmar shahada a matsayin kalmarta ta k'arshe a duniya, an ci kuka har an gode Allah kamar babu gobe, wasu suna son suyi dauriya amma da an kalli yaranta uwa uba Ameera sai a saka wani sabon kuka. Hamna na zaune kan dakalin dake fuskantar cikin asibitin su Zeituna suka fito jiki a mace kowa na ta sharar hawaye, da mamaki ta taso ta tare su cikin dakusashiyar murya tace "Aunty kuma ta saka ku kuka ko? Ni bansan me yasa take haka ba, amma yanzu ya jikin nata?" Kallon juna sukayi sai Hajia da tace "Jikin Amna yayi sauk'i Hamna." Murmushi tayi tace "Taji sauk'i kenan Hajia?" Sake kallon juna sukayi suka mata shiru, kallon kowane take da alamar tambaya tace "Lafiya? Wani abu ya faru ne?" Zeinabu ce tayi k'arfin halin cewa "Hamna ciwon Amna dai ya k'are daga yau." Kallonta take kamar irin bata gane komai a abinda take fad'a, suma duk ido suka tsura mata suga me zai faru, kusan minti d'aya tayi a haka kafin ta fara jinjina kanta, lokacin data motsa sassan jikinta ne kad'ai ta fahimci wasu sabbin hawaye masu zafi dake gangaro mata, nuna kanta tayi da yatsa kamar mai koyon magana tace "Am...na, ye..r uwata, me ya sameta?" Hajia ce ta dafata cikin ban baki tace "Sai hak'uri Hamna, haka Allah ya so, addu'a zaki mata kinji." Wani k'arfi ne taji ya zo mata ta tunkari d'akin da gudu, babu wanda yayi yunk'urin binta a guje sai k'wala mata kiran da suka shiga yi, a lokacin Amar da Jibril sun fito sai cikin ma'aikatan asibitin dake binsu a baya zasu tafi da gawar morgue, yanda suka ji suna k'wala mata kira gashi sunyi karo da ita a k'ofar shiga yasa Jibril k'arfin halin rik'o hannunta, da k'arfin bala'i tasa d'aya hannun ta turashi baya har yayi tangal tangal sai kuma ya tsaya cak, ta, cikin ankarewa da mazantaka Amar ya rik'ota gaba d'aya, dan inba haka yayi ba zata zille masa, k'ok'arin kubcewa ta shiga yi da wani mugun kuka da iya k'arfinta, saida ya rintse idonshi gam ya had'e yawu yayi salati ga annabi sannan yayi k'unar bak'in waken d'ora kanta a k'irjinshi amma jikinta bai had'u da na shi ba, hanya suka basu suka je wucewa da gawar, kukan kura tayi ta rik'e gadon tana shirin bud'e zanin rufar dake jikinta, wannan karan kam k'arfi yasa mata yana son b'anb'are hannunta daga jikin gadon, zubewa tayi zaune ta rik'e gadon gam tana kuka tana fad'in "Wallahi bata mutu, bata mutu ba yer uwata ku sake dubata da kyau, Amna ki tashi dan Allah karsu rufe ki kinji." A lokacin su Hajia suka shigo suma suka fara rik'eta, da tsiya aka rabata da gadon aka turashi aka fita, daga zaunen nan tabi gadon da kallo tana zuwa k'ugunta har ta fuskanci k'ofar fitar, kuka take sosai sai Amar daya sulale ya bar wurin yana mai tausaya mata, take yaji wasu k'walla a idonshi shima daya tuna idan fa shine yau aka ce ya rasa nashi rabin jikin Ammar?. Duk k'ok'arinsu na son su lailayeta zuwa mota su tafi gida sun kasa, sunyi juyin duniya ta k'i basu had'in kai, gashi sun dai babu mai iya d'aukarta, mai iyawa mutum d'aya ne kuma shima baisan a inda yake ba yanzu, hatta lieutenant da ya zo cikin mutuwar jiki bai iya cewa komai ba kallonsu kawai yake suna jata, zuwa Labaran ne kad'ai ya kwakwafeta ya lallab'ata ta tashi suka tafi gida. Hamna kowa yafi tausayinta, tayi kuka kamar ita ma zata mutu, muryarta ta disashe idonta da fuskarta sun kumbura sumtum, ta k'i ci ta k'i sha sai kuka kawai, tana uwar d'akin Amna zaune rumgume da Ameera wacce yanzu ita kad'ai take yarda da ita. Hadiza da Ummy an rasa ina uwar Amna a cikinsu, dukansu sunyi juriya wajen tak'aita mata kuka, Tunda aka kwantar dashi bai sake sanin me ke faruwa ba saida ya kwana ya hantse, tunda ya bud'a ido ya kafe wuri d'aya yana kallo, tashi yayi zaune ya sauko da k'afafunshi, kanshi na kallon k'asa yana tariyar abinda ya faru, a hankali yaji siraren hawaye na fita a idonshi, cikin zuciyarsa yake fad'in "Ta tafi? Da gaske ta tafi? Ya zanyi? Me yasa zata tafi a wannan lokacin?" K'ofar da yaji an bud'e yasa shi d'ago kai amma bai kalli me shigowa ba, har saida suka k'araso suka tsaya kanshi suna kallonshi, a hankali Junaid yace "Ammar ya jikin na ka?" Cikin girgiza kai yace "Ni ma ban sani ba?" Amar ne ya zauna kan gadon yana kallonshi yace "D'an uwa, kayi hak'uri kaji, dama duk..." Katseshi yayi da cewa "Ina take?" Shiru sukayi na dak'ik'u kafin Jibril yace "Gidanta na gaskiya." Lumshe ido yayi, muguwar yunwar da yake ji ce ta had'u da wani zafin zuciya da yaji ya taso mishi, dafe k'irji yayi da d'aya hannu kua yana matsar cikinshi, ba tare daya bud'e ido ba yace "Me yasa baku bari na mata kallon k'arshe ba? Ina son ganin kyakyawar fuskarta." Dafa kafad'arshi Amar yayi yace "Kayi hak'uri Ammar, ka mata addu'a shine soyayyar da zaka nuna mata." Jinjina kai ya shiga yi kamar k'adangare yana fad'in "To, to naji, zan mata." Bud'a ido yayi ya zura k'afafunshi ya sauka daga kan gadon, jiri ne ya d'ebe shi yayi gefen da Junaid ke tsaye kamar zai fad'a masa, da sauri ya rik'e shi yace "Sannu, Ammar jiri ke damunka ka kwanta ka huta mana." Amar ne ya kalleshi yace "Ina ga fa kamar harda yunwa, mu kaishi gida sai a samar masa wani abu ya ci." Zamewa yayi daga rik'on da Junaid ya masa ya nufi k'ofa, layi yayi tare da neman fad'uwa a wurin Amar yayi saurin rik'eshi ta baya, saida ya gyara shi da kyau ya matseshi a hannunshi suka fita a d'akin. Gashi dai zaune yana kallon mutane amma tunaninshi da hankalinshi na wani wurin daban, rayuwa bata da tabbas, ya gamsu ya rasa wani b'angare na jikinshi, ta tafi ta barsa da yaran da kullum ya kallesu zai tuna da ita, ta zauna dashi cikin aminci, tayi zama dashi zaman daya zama a tarihi a cikin rayuwarsu, ta mishi alkairin da shi dai bai ga abinda zai iya saka mata dashi ba, addu'a, addu'a ce kawai abu mai mahimmancin daya rage tsakaninshi da ita. Tun yana zama a wajen makokin har zazzab'i ya ci galaba kan shi ya kai kanshi d'akin maganinshi ya burmawa kanshi allura, anan ya kwanta kan gadon dake d'akin yana tuna ranar da Hajia ta yanke hukucin aurensu, ranar auren ta su da irin zamantakewarsu har ranar data yi nak'uda kan gadon nan da yake kwance yanzu. _Lumshe ido yayi hawaye suka shiga sintiri kan fuskarshi, ba tare daya bud'a ido ba ya hasko ranar da yace mata "Duniya ta yanzu idan nace zan k'ara aure dan Allah ya zakiyi?"_ _Dariya ta masa tace "Ya zanyi kuwa daya wuce na tayaka k'wato zuciyar ko ma wacece har kayi nasara."_ _Had'e fuska yayi yace "Kenan ba zakiyi kishi na ba?"_ _Sajenshi ta shafa tace "Zan yi mana, amma ba irin wanda kake tunanin zan yi ba."_ _Hannu ya d'aga kamar zai mareta yana fad'in "Dallah can malama, ni da nake so kiyi tashin hankali ki hana ni ko da shan iska."_ _Da k'arfi ta cakume shi ta kamkame jikinshi tana fad'in "Yi hak'uri yah Ammar, karka dake ni dan Allah, zanyi kishinka wallahi."_ _Dariya ya mata ya rumgumeta sosai a jikinshi, cikin muryar shagwab'a tace "Yah Ammar zani kishinka sosai, amma ba zan yarda na tayar maka da hankali ba saboda kishi, ni dai kawai so nake ka min alk'awarin ko da ka sake aure ba zaka wulak'anta ni ba."_ _Cikin laushin murya yace "Me yasa kike tunanin zan wulak'anta ki Amna?"_ _"Saboda ba ni ce zab'inka ba, kawai Hajia ce ta had'a mu."_ _Rumgume ta ya sake yi yace "Karki damu duniyata, ina sonki har zuciyata ba zan wulak'anta ki ba."_ Bud'a ido yayi ya tashi zaune duk k'ok'arinshi na son tare kanshi saida ya kasa ya fashe da kuka, wallahi a lokacin da za'a bashi zab'in rayuwa ko mutuwa daya bita shima su rayu acan, bansan taya zaiyi rayuwa bane yanzu babu ita, ita ke saukar dashi k'asa idan yayi samada k'arfin tsiya, an kai an kawo lokacin da Amna ko fita zaiyi waje saita gargad'e shi ya kiyaye abinda zai sa ranshi b'acewa, baiwar Allahn nan ta zab'i ya daketa ko da zai ji mata ciwo akan ya fita ranshi a b'ace yaja rigima, duk da ta kare shi ta kare mutumcin shi, to yanzu wa zai mishi wannan gatan? Wa zai bashi wannan kulawar? Ya rasa kenan har *abada*. _*Allah ya jik'an duka mamatanmu ya gafarta musu, Allah ka kai rahama k'abarin iyayenmu mata har da ma mazan, mutuwa irin ta Amna Allah ka basu ladar shahada, Allah ka kyautata namu k'arshen.*_ *A gurguje* Sanyi sosai kamar agogon da batirinsa ya k'are haka al'amarin ya zama a wajen Ammar da Hamna, shiru da zuba ido shi yafi yawa a cikin rayuwarsu ta yanzu, idon Hamna har sunyi fari fat tsabar yawan kuka da rashin saka kwalli, in dai har yaran zasu kewaye ta saita zubar da hawaye ta kuma aika mata da addu'a, kular da take basu kamar daga cikinta suka fito, a dalilinsu ta aje zuwa salon, tace bata da abinda ya kaisu bare ya kai daidai da su, idan ta tashi tun asuba tayi sallah, haka zata musu wanka ta shirya su cikin kayan makaranta, da kanta ta ke kaisu a motarta kuma taje ta d'aukosu, abinda suke son ci shi zata girka musu da kanta, idan na siyowa ne ta siyo musu da kud'inta, a tak'aice dai ta zama uwar yaran wacce ta haife su. *Ahmad* dama tanti Hadiza aka yanke shawara aka barwa ta tafi dashi, amma duk sati biyu sai Hamna ta tafi da yaran sun gano shi, wani lokacin har kwana suke a can kafin su dawo. Girmanta ya k'aru a idonshi da kuma soyayyarta, yanda take d'awainiya da duka yaran yana birge shi sosai, ko Shureim bata da lokacinshi kamar su, hankalinshi kwance yake akan yaran, ko kud'in makarantarsu shi dai bata tambayarshi sai in anyi katarin ya ga takaradar a aljihun rigar Ameer sannan yaje ya kai da kanshi, sai dare idan ya dawo suke zuwa inda yake su sha hirarsu shi dasu su mishi kwaramniya, inda kowane giftawa nasu yana tuna mahaifiyarsu ne, hak'urinta akan yaran ya wuce misali, duk yaanda yaro zaiyi k'ololuwar rashin ji bakinta dashi sai dai tace "Wallahi zaneka zanyi." Kuma ba.zata zanesu d'in ba, Allah sarki, yau gashi ta barsu zasu tashi da maraicin uwa, shi a ganinshi ma har da uban, dan uwar ita ce tasa ya zama uban, uban ma kamili da zai iya amsa sunan uban a gaban ko waye, to yau bata nan sai su kad'ai. *Sanda* rayuwar ke tafiya a haka a lokacin kuma Hajia da Ummy da Husseina suka zaunar da Abba suka sanar dashi fa Shureim d'an Ammar ne, tunda yake a rayuwa bai tab'a jin an ci mutumcin shi an muzanta shi an wulak'anta shi irin na yau ba, wannan yafi k'arfin k'arya har da yaudara da cin amana, ta ruguza zumuncin dake tsakaninshi da d'an uwanshi, rainin wayon da rainin hammatar ma yayi yawa, haka a wannan rana ya ci fad'a ya gode Allah, yayi kamar zai dake ta abinda bai tab'a yi ba, a k'arshe kuma ya juya mata baya inda yace Ammar baida laifi sai ita. *Kwana tashi* yau kimanin wata shida kenan da rasuwar Amna, inda kowa ya darrafe yayi hak'uri ya barwa Allah, yara sun tafi école (school) sun dawo ba ayi, suna d'aki tare da Hamna tana canza musu kaya, cikin farin ciki Ameera tace "Ummy." "Na'am yar Ummy." Hamna ta amsa dashi, cike da yarinta tace "Yau tunda bamu école zaki kaimu wajen Abban mu?" Da mamaki ta kalli fuskarta tace "Abbanku kuma? To ba yana gidan ba? Kuma jiya ba kunje wajensa da dare ba?" Turo baki tayi "Ai Abba ne yace idan bamu karatu zai tafi damu yawo." Shafa kanta tayi tace "To yanzu ai yana wajen aiki ko baby." Mak'ale kafad'a tayi tace "To mu dai ki kaimu wajenshi ko ki kira shi ya zo ya d'auke mu." Kallon fuskar yarinyar tayi sosai, d'an matse bakinta tayi a hankali saboda tunawa da tayi da mahaifiyarta, sauke numfashi tayi ta mata murmushi tace "Shikenan baby Ameera, a gama saka kayan sai mu tafi ko." Cikin jin dad'i tayi dariya, ita ma murmushi ta sake mata ta k'arasa shiryata, su Ameer ma k'arasa shiryasu tayi cikin shiga mai kyau, a tare suka fita ta nemi izinin Hajia sannan suka fita, tana shiga mota wayarta dake hannun Ameer yana game ta shiga ruri, mik'o mata yayi ta karb'a ta ga Hadiza ce, tana d'auka suka gaisa tace mata "Kina gida ne?" "Eh Mama, lafiya?" Daga b'angarenta tace "Lafiya lau, dama ina hanyar zuwa ne zan kawowa su Hajia Ahmad su ganshi, kullum sai sun kira ni sun tambaye shi." Cikin farin ciki tace "Ummy Ahmad? Yanzu zaku taso ne? Nima ina son ganinshi wallahi." "Wace tasowa kuma Hamna, yanzu haka fa ina cikin adaidaita har mun shigo layin gidan." Fitowa tayi daga mota tana fad'in "Lah Mama, kinga kuwa da fita ne zamuyi, ku k'araso to." K'ofar gidan ta fita inda yaran suka bita, ko da adaidaita ta aje ta yaran sukayi caa a kanta, tana kawo musu kayan motsa baki shiyasa ta gama siye zuk'atansu (yaron kenan), Hamna karb'ar Ahmad tayi tana ta sumbatar yaron tana kallonshi, masha Allah ya mulmuje sosai fuskarshi ta fito sak ta mahaifinshi, an shirya shi cikin riga da jeans na yara masu kyau ga takalmi gwanin sha'awa, kallon Mama tayi ta marairaice tace "Mama, yanzu haka wajen Abbansu ne suka matsa na kaisu, dan Allah ki barmu mu tafi dashi, nasan zaiji dad'i idan ya ganshi shima." Zaro ido tayi tace "Hamna kina lafiya, daga zuwanmu ko ciki ban shiga dashi ba ki ce zaki tafi dashi?" Cikin muryar rarrashi tace "Mama, wallahi ba jimawa zanyi ba, ina kaisu zan juyo na dawo, zai fita dasu ne kinga idan ya ga Ahmad ni sai na dawo tare dashi, dan Allah Mama." Cike da gamsuwa ta kalleta cikin kashedi tace "To Hamna kamar yanda kika ce dan Allah karki jima, nasan zan sha k'orafi wajen Hajia da Sa'ada, amma zan yi yak'i indai akan wannan d'an gudaliyar ne." Da farin ciki tace "Wallahi ba zan jima ba, mun gode Mama." Tare suka shigo ita ta shiga mota tare da yaran, zaunar dashi tayi kan kujerar gaba tare da Ameera ta manna musu d'amarar jikin kujerar sannan suka bar gidan. Ya gama ganin majinyatanshi yana zaune da wasu takardu yana dubawa aka k'wank'wasa k'ofar, yaran basu jira izini ba Abba ya tura duk suka shiga, saida suka gama shiga ya taso da farin cikin ganin yaran ya duk'a duk suka rumgume shi, cikin murna yace "Waya kawo ku ne?" Kafin su bashi amsa ta zuro k'afarta d'auke da Ahmad, cikin sanyayar muryar tace "Assalama alaika." D'ago kai yayi ya sauke tanfatsa tanfatsan idonshi akanta, tsayar dasu yayi ko su suka tsaya da kansu sani sai Allah, amma ta mugun tafiya dashi da imaninshi baki d'aya, mik'ewa yayi a hankali ba tare daya d'auke idon ba, saida ya gyara murya sannan yace "... *Alhamdulillah* _Wallahi yau na gaji_ 04/11/2020 à 14:38 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _65_ "Ke ma haka." Shine abinda ya fad'a yana k'are mata kallo, da sauri ya tako ya zo ya karb'i Ahmad a hannunta, rumgume shi yayi a jikinshi yana satar kallonta, da d'an mamaki yace "Mama ta zo kenan? Amma ya bata sanar dani ba? Kuma daga ina kuke?" Ba tare data kalleshi ba tace "Daga gida, sun ce na kawo su ne kace musu zaku fita." Girgiza kai yayi yace "Halan Amna ce?" Sak'e tayi ko da taji ya ambaci sunan, ita ta ma rasa dalilin da yasa shi sanya ma yarinyar sunanta, ba tace komai ba sai shi da yace "Ita ce bata da mantuwa ko kad'an." Ita dai idonta na kan yaran dake ta k'iriniyarsu, shi ma damar sake kallonta ya samu, tayi kyau sosai cikin doguwar rigar atamfarta mai kalar maroon da ratsin orange da bak'i, mayafin d'an babba ne ta rufe duka k'afad'unta da shi, babu jaka ko waya a hannunta kamar yanda babu powder bare kwalli a idonta. Kallon idonta yayi yace "Zauna ko." Ba tare data kae shi ba tace "Zan koma gida ne yanzu, Mama na jira na." "Yau zasu koma ne?" "Eh." Ta fad'a kanta a k'asa, d'aga gira yayi yace "To ki jira ni kad'an sai mu tafi tare, nima yanzu gidan zan tafi." Da sauri tace "A'a, Mama ta yarda na taho da Ahmad ne saboda na ce ba zan jima ba, ko ciki bata shiga dashi ba na karb'o shi." "Me yasa?" Ya fad'a yana kafeta da ido, sai lokacin ne kawai ta d'an d'aga idonta ta kalle shi, ya d'anyi rama sai gemunshi daya k'ara cika fuskarshi, saurin kawar da idonta tayi saboda kwarjininshi tace "Na d'auka kana son ganinshi ne." Murmushi yayi yana kallon labb'enta masu duhu, mamakin yanda ta canza yake sai wani sunne kai take bata so su had'a ido, juyawa yayi ya zauna kan kujerar shi yaran duk suka zagaye shi kowa da abinda yake tab'awa, kallonta yayi yace "Nagode fa." Wutsil wutsil tayi da ido kamar mai son tuna abinda ya faru yanzun har yake mata godiya, cikin nutsuwa ta d'aga duka idonta ta sauke kanshi tace "Godiya akan me?" Kallonta yayi yace "Akan kulawar da kike da yaran nan." Cikin sunkuyar da kai tace "Dan na kula da yara na har ina buk'atar a gode mun ne?" Cike da jin dad'i yace "Yaba kyauta tukuici mana." D'an tab'e baki tayi kawai ko kallonshi ba tayi ba, murmushi yayi ya mayar da hankalinshi kan yaran, ganin sun fara hira zai manta da ita a tsaye yasa ta d'anyi gyaran murya, a hankali ya juya ya kalleta da alamar tambaya, kamar marar gaskiya ta kalle shi tace "A..h.mad, zamu koma ne." Ajiyar zuciya ya sauke ya taso daga kan kujerar, saida ya zo daf da ita ya mik'a mata shi, tana karb'arshi ta kalli yaran tace "Sai kun dawo gida." Juyawa tayi sai kuma yace "Kin manta." Juyowa tayi sai kawai ya karb'o wayarta a hannun Ameer ya mik'a mata, kallon fuskar Ameer tayi sai taga duk bai ji dad'i ba, kallonshi tayi tace "Ka bashi ya ci gaba da wasanshi, idan kun dawo gida saina amsa." Ba alamar wasa yace "Ita d'in ai ba abar wasa bace, ya kamata kuma ki fara nuna musu cewa rayuwa ba komai kake so kake samu ba." Yana fad'a ya danna mata ita a hannunta. Kallon fuskarshi tayi amma ba cikin idonshi ba tace "Hakane, amma ai abinda ya shigo hannunka da wanda ke hannunka bai kamata ka bari ya kubce maka ba, shi ta riga data shiga hannunshi, ka bar masa kawai zan karb'a ba ta yanda ranshi zai sosu ba." Wani shu'umin kallo ya mata had'e da murmushi yana motsa labb'enshi a hankali yace "Wannan soyayyar da kike nuna wa *Ammar* fa tana yawa." Kallonshi tayi sai ta fahimci iskanci ne ya soka mata, ita ma d'an murmushi tayi tace "Ina son k'aramin Ammar sosai, ba shi kad'ai ba duka yaran da suka fito daga cikin babbar Amna ma." Murmushi yayi sosai ya k'ura mata ido, kallonshi tayi tace "Sai anjima." Bai ce komai ba har ta juya zata fita yace "Me yasa? Yana ina?" Tsayawa tayi ta juyo ta kalleshi tace "Waye?" Ba tare daya rusuna idonshi ba yace "D'ana Shureim." Tab'e baki tayi tace "Yana gida mana." "Me yasa baki taho dashi ba? Ina so naga duka iyalina a tare dani, shi kad'ai ne babu a wurin nan." "Idan ka cire ni ba." Ta fad'a kai tsaye, murmushi ya mata mai ban mamaki yace "Har da ke mana, fuskarki fuskarta ce." Kallonshi tayi fuskarta babu walwala, juyawa tayi zata fice taji muryarshi cikin isa da zarra da k'asaita yace "Kiyi sauri ki kawo min shi shima ina buk'atarshi anan." Juyowa tayi tace "Kayi hak'uri, gaskiya idan na shiga gida yanzu ba zan fito ba." Kallonta yayi cikin rikid'ewar lokaci d'aya yace "Ki kawo min shi nan da minti ashirin ina jiranki, inba haka ba saina daddala miki mari wallahi." "Mari fa? A wannan k'arnin?" Ta fad'a cike da rashin tsoro, cikin tabbatarwa yace "Ki jaraba ki gani to, ba zan tab'a yin kaffara akan abinda nake da yarda akaina a kan shi ba." Girgiza kai tayi tace "Ba zaka tab'a canzawa ba har abada." Ba tare daya kalleta ba yace "Zan canza ranar da kika so hakan." "Kamar ya?" Saida ya zauna kan kujerarshi ya kalleta yace "Kamar yanda kika ji na fad'a." Juyawa kawai tayi suka fice ta barsu, da kallo ya bita shima har ta fita, bai kammala abinda yake ba ya fita da yaran dan yana so ya dawo kafin rana ta sake takewa sosai. Shigar Hadiza ciki ko gaisawa basu gama yi ba gwamna ya zo gida, cikin rakiyar masu tsaron lafiyarsa har ya shiga falon kafin suka barshi, nan aka shiga gaisawa har da Hadiza saida suka gaisa cikin mutuntawa ba tare da idonsu sun had'u ba, sun gaisa da kowa amma banda lieutenant da Sa'ada. *Ummy* kuma ta riga Hamna fita a gidan, dan a lokacin da taje dan suyi magana da lieutenan akan banzan da yake yi da ita, tana so ya fad'a mata matsayinta, tunda abun ya faru baya ko kallonta, ya daina zuwa d'akinta ranar kwananta sai dai ita taje, idan ta je kuma ko magana baya mata hasalima wani lokacin sai yace ta bashi wuri yana son zama shi kad'ai ko zaiyi wani abu, abun ya dameta sosai ta yanda yanzu ko gaishe shi tayi gaban mutane sai dai ya amsa da lafiya ko yawwa, har ta lura da mutane sun ankara da rayuwar da suke yi yanzu, dan haka safiyar ta yau taje har d'akinshi dan ayi ta ta k'are, wata shida ba kwana shida bane ai. Sanda ta je ta same shi yana shirin fita dan yau baida fita da wuri, sallama tayi ya amsa da k'yar ba tare daya kalleta ba, saida ta tsaya d'an nesa dashi tace "Ina kwana." Shiru yayi yana ci gaba da saka rigarsa ta kakinshi, ko da ta ga zai b'alla botira tayi saurin matsawa zata taimaka masa, baya yaja tare da k'ara had'e fuska a cikin mak'oshi yace "Um um." Kallonshi tayi tare da sauke hannayenta k'asa tace "Magana na zo muyi idan kana da lokaci?" Shiru ya mata ya ci gaba da shirinshi kamar baisan da zamanta a d'akin ba, zaune yayi kan kujera yana d'aura d'amarar takalminshi, hakan ne ya bata damar matsowa tace "Magana nake." K'asan mak'oshi sosai yace "Aiki ya min yawa yanzu bana da lokaci kaina ma, ki gaggauta fad'in abinda ya kawo ki." Saida ta gyara tsayuwarta sosai sannan tace "Tunda abun nan ya faru ka canza min, na baka hak'uri har na gaji, Hajia da su Hajiar Jibril ma duk sun tayani baka hak'uri, amma abinda na fahita shine baka hak'ura ba har yanzu, a gaskiya na fara gajiya da irin halin ko in kular da kake nuna min, shine nake so ka fad'a min a me kake kallo na ne? Sannan me ye matsayi na a wurinka yanzun?" Cike da nuna rashin damuwa kan maganar ya d'auki hularshi ya saita zamanta yana fad'in "Duk irin zaman da kike tunanin kina yi shi kike yi." Jakarshi ya d'auka zai fita tayi saurin tare da gabanshi tace "Wannan wace irin magana ce? Abban Ammar ka tsaya muyi magana." Kallon fuskarta yayi cikin yanayin firgitarwa yace "Na gama magana ni ba zan b'ata lokaci na anan ba." Zai fita ta rik'e hannunshi tace "Nima ina so na kawo k'arshen abun ne, dama zamanka na ke a gidan nan, idan ka juya min baya banga anfanin zaman nawa ba." Shiru tayi ta ja numfashi sosai sannan ta ci gaba da cewa "Ina so ka min magana d'aya kuma tsayayya, idan ka gaji da zama dani ne to na san inda dare ya min? Tunda kafi kowa sanin inda ka d'auko ni ai." Ba tare daya kalleta ba yayi murmushi mai ciwo yace "Ni kuwa nasan inda na d'auko ki, da kai tsaye kika fito kika fad'a min abinda kike so, amma..." K'ofa ya nuna mata yace "Hanya a bud'e take ban rik'e miki k'afa ba, zaki iya tafiya ko yanzu ma." Zai wuce ta sake rik'oshi da k'arfin da Allah ya hore mata tace "Ba zan tafi ba tare da shaidar komai ba, tunda haka ka ce to ka ban takardar da zan nuna ta zama hujjar tafiyata kenan, dan in na tafi ma bana son dawowa." Kallonta yayi yace "Kije zan aika miki da ita, yanzu bana da lokacin tsayawa rubutu." 😂 *Maza mutanen mu, mu ke shayar daku amma in kuka labta mana wata tsiyar...hummm* Da sauri tace "Zan tafi yanzu, amma ka sani ina jiran takardata gobe goben nan." Wucewa yayi yana fad'in "Anfanin me ma zata miki yanzu ko an baki? Ina ce zaki koma gidan nan da ki ci gaba da kulawa da yan uwanki." Da kallo ta bishi tace "Ita ce lasisin fara zawarci na." Duk da bai tsaya ba saida ya juyo ya kalleta ya kuma ci gaba da tafiya, zawarci? Matarshi ta shekara arba'in ba kad'an? Tayi zawarci har ta auri wani? Maganar fa ta soke shi sosai, ba dan baya son kulata ba da saiya buge bakinta, tunda dai har yanzu yana son abarsa kawai kuskurenta ne zai nuna mata, dan har ranshi yayi rantsuwa daya san abinda ya faru a lokacin *wallahi da sai Ammar yaje gidan maza* kan abinda ya aikata, yanzun ma wuri bai k'ure ba sai dai wacce zata zama tsayayyar shaidar ita ce Hamna, kuma yana tsoron shak'uwa ta yan uwantaka da jinin shi dake yawo a jinin jikin d'anta yasa ta basu kunya, shiyasa yayi fatali da maganar Ammar kawai. Ai kuwa Ummy da gaske take, ko da ta shiga d'aki kayanta ta had'a a jaka ta fita a gidan ko Hajia bata san da fitarta ba. Lieutenant kuma ya d'an jima d'akin Zeituna hakan ne yasa ko da ya fito ya samu d'an uwanshi ya zo da kuma Hadiza zaune suna gaisawa, Hadiza ce ta kalleshi cikin girmamawa tace "Ban ga Sa'ada ba ni ko har ta tafi aiki ne?" Juya akalar zancen yayi da cewa "Ina mutumen ne (Ahmad)?" Da murmushi tace "Ai ina zuwa uwarshi ta karb'eshi, tace ta tafi ta kaisu wajen Abbansu amma yanzu zata dawo." Jinjna kai yayi sai Hajia data sake cewa "Babba ina Sa'ada? Yau kamar ba ranar aikinta ba ai?" "Ta tafi." Yanda ya fad'a fuska a gimtse yasa Gambo kallonshi yace "Asibiti?" Shirin daya musu ya tabbatarwa da Hajia ba lafiya ba, dan haka tace "Ina? Tana ina Babba?" Cikin sanyin murya yace "Hajia ta tafi, nima ban sani ba." "Kamar ya baka sani? Babba zauna." Zaune yayi ya aje jakarshi gefe ya kalleta, cikin rashin son wasa tace "Fad'a min ina taje da safiyar nan? Ni dai banga sanda ta fita ba." Ba tare daya had'a ido da ita ba yace "Hajia ta tafi, akan abinda ya faru ne, ita ce mai laifi ma amma har ta tsaya gabana tana fad'in idan na gaji da ita ta tafiyarta." "Sai ka ce mata me?" Cewar Hajia, saida ya waina kanshi yace "Shine ta tafiyarta, tace na aika mata da takardarta." Da k'arfi Hajia tace "Babba, kana da hankali kuwa? Yanzu kai baka ji kunyar fad'ar maganar nan ba? Matar ta ka?" Gambo dake kallonshi da mamaki ne yace "Wai me ya faru ne haka da zafi? d'an uwa a sani na daku baku tab'a samun sab'anin da yasa tayi ko da yaji ba, me yayi zafi haka da girmanku da komai kuna fad'an yara." Kallon Hajia yayi ranshi a b'ace yace "Hajia ni zan tafi." Mik'ewa yayi zai fita Hajia tace "Ban gama magana da kai ba zaka mik'e min a kai Hassan, zauna min kaji malam." Muryar da tayi magana da ita ta waccen Hajiar ce, dole ya dawo ya zauna yana sunkuyar da kai, Hadiza kam mik'ewa tayi ta kalli Hajia tace "Hajia zan jira a waje, akwai buk'atar ku tattauna." Cikin mutumtawa Hajia tace "Zauna Hadiza, ai ke ma har yanzu iyalin gidan nan ce." Murmushi tayi tace "Ban k'i ta taki ba Hajia, amma duk da haka akwai buk'atar kuyi magana tsakaninku." "Hadiza karki manta fa yara biyu ne dake wanda kika samu a gidan nan, sannan abinda ke faruwa yanzun yana da alak'a da d'aya daga cikin ya'yan naki, ki zauna dan Allah sai muyi magana." Komawa tayi ta zauna gabanta na fad'uwa kan abinda Hajiar tace, kallon lieutenant tayi tace "Kira min Sa'ada ka ce inji ni duk inda take yanzu ta zo ina nemanta." Wallahi wannan Hajiarsu ce ta baya mai magana d'ayan nan, in yayi wasa zai sha ashar yanzu dan haka da sauri yace "To." Wayar shi ya fiddo ya shiga neman lambarta, Gambo ta kalla tace "Ka kira min Ammar ka ce ya zo." "To." Ya fad'a yana ciro wayarshi a aljijun balaluwarshi, yana gama magana dashi a lokacin har ya fita da yaran, sake umartarshi tayi daya kira Hamna sannan ta kalli Hadiza tace "Husseina na ciki, ki ce ta fito zamuyi magana." "To Hajia." Ita ma ta fad'a ta nufi d'akin jikinta har rawa rawa yake na tunanin abinda ya faru tsakanin Ammar da Hamna daya har yasa Ummy suke k'ok'arin rabuwa da lieutenant. Hamna ma ko da kiranshi ya shigo wayarta tana k'ofar gidan, saida hancin motar ta ya shigo sannan ta d'auki wayar, shi kuma yana hangenta ma saiya kashe kawai. _Kuyi hak'uri da wannan, yau ne sai a slow._ *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:38 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _66_ Husseina ta fito ta samu wuri ta zauna, tunda sauran matan suka fahimci zaman ba dasu bane kowace tayi d'akinta, sai lieutenant dake kiran Ummy, k'in d'aukar kiranshi tayi tunaninta hak'uri zai bata, Hajia ya kalla yace "Hajia ta k'i d'auka fa." Wayarta ta lalubo a bayanta tana fad'in "Ban ga laifinta ba mana." Kallon Hajiar yayi da mamaki, wai duk abinda tayi bata ganin laifinta? Kiran Hajia kad'ai ta d'auka cikin ladabi tace "Hajia." Kai tsaye tace "Kina ina Sa'ada? Maza ki zo gida ina son ganinki." Cikin rarrabawa tace "Hajia..ina..kan hanyar...zuwa gida ne." "Wane gida? Sa'ada kina da gidan daya wuce nan ne? Kina da hankali kuwa? Ke yanzu dan Allah idan kika je ki ce me? Yaji kikayi? Kiyi sauri ina jiranki yanzu." Cikin ladabi tace "Wallahi Hajia da gaske na ke, ina cikin bus d'in da zata tafi *Arlit*, yanzu haka mun wuce *Tessaoua*." Shiru Hajia tayi tana kallon lieutenant da shima yake kallonta yana sauraren abinda take fad'a, sunkuyar da kanshi yayi k'asa ita kuma ta harare shi, wata shawarar ta yanke kawai bari ta barta yaje har can ya dawo da ita, kashe wayar tayi cikin fad'a tace masa "Ka shirya tafiya yin bikonta gobe goben nan, babu ruwa na da iskanci kaji na fad'a maka, kai in ba'a hak'uri da ko haihuwarku nayi a gidan ubanku ma." K'wafa tayi mai k'arfin gaske dake nuna ranta ya b'ace sosai, kafin wani yayi magana Hamna ta shigo tare da Ahmad, da mamakin ganin mahaifinta taje gabanshi ta zauna tana fad'in "Abba? Yaushe ka zo?" Kallonta yayi yace "Banjour." Lab'e baki tayi tace "Pardon Abba, bonjour." Gaisawa sukayi sosai inda take kallon mahaifiyarta da mahaifinta tana jin kamar ace babu aure kan mamanta ta sake had'a aurensu, ba wai sai iyayenka sun mutu ba wani lokacin kake zama maraya, su kansu akwai abubuwa dayawa wanda sukayi musu manqué musamman daga mahaifi, lallai Ummy ta kai su kirata uwa dan ta musu abinda ta cancanci hakan, amma duk da haka uwa uwa ce, ko hakk'in rayuwa a cikinta kad'ai ya ishi d'awainiya dasu. Sallamarshi tasa ta gyara zamanta ta tank'washe k'afafu ta matsa daf da k'afafun mahaifinta, yaran duk wurin Gambo suka nufa ya sumbaci kowane kafin yace suje sama suyi wasa zai zo ya ba kowa tsarabarsa, saida suka haye sannan Hajia ta kalli kowa tace "Abinda yasa na tara mu anan dama akan maganar yaran nan ne." Yanda ta k'arashe maganar da nuna Ammar da Hamna da hannu yasa su k'ura mata ido, dukansu kallo ne suke mata suna tunanin hannun da zasu iya begeta dashi daga lokacin data tona musu asiri, ba tare data damu da kallon da suke mata ba tace "A gani na tunda Hamna har yanzu bata da wani tsayayye me zai hana mu had'asu aure da Ammar?" Kallon kallo aka shiga yi sai dai wasu na su kallon farin ciki da al'ajabain maganar ne, Ammar Hamna kuma a d'an birkice suka fahimci abun, Gambo ne yace "Masha Allah, gaskiya Hajia wannan tunani ne mai kyau." Hadiza ma murmushi tayi tace "Gaskiya ne, Allah ya tabbatar mana da alkairi." Lieutenant da fuskarsa ke had'e yana kallon Ammar ne yace "Amma Hajia ina ga da an ji ta bakinsu, tunda shi yayi rayuwar auren nan yasan komai dake cikinta, ita kuma bata tab'a ba dan haka da an tambaye su aji idan hakan ya musu." Husseina ce tace "Hakane kuma, tunda babu yaro a cikinsu da za'a ma tilas." Hajia ce ta kalli Hamna tace "Hamna kinji abinda aka ce, Me ye ra'ayinki? Ki fad'a mana abinda ke ranki dan ba za'a miki tilas ba." Daram! Gabansu ya fad'i a tare, kallon juna sukayi kowa da abinda yake sak'awa a ranshi, Hamna a ganinta ba zata iya zama da tsohon mijin yer uwarta ba, taya ma zata iya auren yar uwarta saboda ta mutu? Mijin ma kuma Ammar wanda zata iya rantsewa da Allah ba zasu tab'a zama lafiya ba kamar yanda suka zauna da yer uwarta, gaskiya ba zata iya ba sai dai suyi hak'uri. Kallon da yake mata kallon son gane abinda ke ranta ne, bakinta yake kallo yana mai matuk'ar zak'uwa da son jin kalamanta, sanda kanta tayi k'asa tana wasa da yatsunta na hannu, Hadiza ce ta kalli fuskarta tace "Hamna kiyi magana mana, duka anan babu bak'onki." Husseina ce tayi murmushi tace "Ai mace kunya ne da ita, shirun kuma shi ya bamu amsar tambayarmu." Da sauri Hamna ta d'ago ta kalleta tace "A'a Hajia, gaskiya ni ina da saurayi, yanzu ma ni yake jira na bashi dama ya gabatar da kanshi." Tana fad'a ta d'an kalle shi, da sauri ta d'auke idonta, ba zata iya yarda ta k'ara kallonshi ba, wannan kallon babu alamar arzik'i a ciki. Hajia da bata ji dad'in abinda ta fad'a bane tace "Amma Hamn..." Ammar bai jira me zata ce ba yayi saurin cewa "Nima haka, ina da wacce nake so." Ko da ya fad'a ya mik'e tsaye ya juya zai fita Gambo yace "Ammar dawo ka zauna." Juyowa yayi cike da girmamawa yace "Dan Allah tonton, zan gabatar muku da ita nan da lokaci k'ank'ani." Juyawa yayi ya fice ita ma a hankali ta mik'e zata shiga d'akinta, duk sai taji jikinta yayi sanyi da yace wai yana da wacce yake so, lallai ma mutumin nan! Kenan har ya manta da yer uwarta a wata shida kacal ya fara son wata? Tsaki tayi a zuciyarta tana fad'in "Allah ya tsine mata ma." 🤔 *Wacece?* Gambo ne ya katse mata tunaninta da tafiyarta ta hanyar fad'in "Ke." Juyowa tayi ta dawo ta durk'usa gabanshi, cikin kakkausar murya da gargad'i yace "Tunda kince baki son d'an uwanki to ki turo mana wanda kika ce d'in, yau d'in nan ba zan bar garin nan ba sai nayi magana dashi." A mugun tsorace ta kalleshi, me kenan ta jawo ma kanta? Ita fa ta fad'a ne dan abar maganar shi, amma bata da wani tsayayye yanzu ita in banda 'yan abi yarima asha kid'a, yanda ta kakkafeshi da idonta babu ko k'yabtawa yasa shi daka mata tsawa cikin jin haushi yace "Tashi ki bani wuri, kina girma kina cin k'asa har yanzu kin kasa sanin ciwon kanki." Saida ta juya zata tafi taji wasu hawaye sun taho mata, bata san abunyi ba a yanzun gaskiya, Hadiza ma da bata ji dad'in k'in amincewarta ba tashi tayi tana fad'in "Kuyi hak'uri dan Allah zanyi magana da ita." "Dawo zauna Hadiza." Cewar Hajia, komawa tayi ta zauna tana kallon Hajiar da tace "Watak'ila tana da dalilinta na k'in amincewa, karku matsa mata dan Allah ku barta ta zab'arwa kanta abinda take so." Gambo ne yace "Amma Hajia ko ma menene dalilinta ai bata k'i d'an uwanta ba, ko dan marayunshi ai zata amince." A hankali Hajia ta kalli lieutenant ta kuma kalli Husseina, kallon Gambo da Hadiza tayi tace "Magana ta gaskiya bai kamata mu ci gaba da b'oye muku ba, ku kuka haifi abarku ya kamata kusan komai dake faruwa kan 'yarku." Gaban Hadiza ne ya sake fad'uwa dan ita tun farko tayi tsammanin jin wani mummunan abu, kallonta suke sosai kafin ta gyara zama tana fuskantarsu da kyau tace "Kuyi hak'uri dan Allah ku yafe mana dukanmu, sannan zan so ku nutsuwa kuyi duba na tsanake akan lamarin, karku yanke hukunci cikin hushi, hakan zai iya janwo mana dana sani." Shiru tayo sai Hadiza da tace "Hajia ko me ya faru bai kamata ace kina neman afuwarmu ba, mu 'ya'yanki ne baki buk'atar wannan." Gambo ne yace "Hakane, koma menene Hajia ai ba sai kin rok'e mu ba." Numfasawa tayi cike da muryar rarrashi da nuna nadama tace "Shekara biyar da rabi kenan da wata mummunar k'addara ta fad'a kan Hamna, idan kaji ance tsautsayi to akwai ganganci a ciki, shi yasa na ce muku k'addara dan ku fahimta da kyau, k'addarar data tashi fad'a mata ma sai ta fito daga ruhin d'an uwanta Ammar, bayan abinda ya faru ya faru ciki ya shiga jikinta, hakan kuma ya tabbatar mana da lallai wannan abun daya faru rabon wannan yaron ne, dan da wani yayi k'ok'arin shiga tsakanin faruwar wannan al'amari, ko shakka babu wannan rabon zai iya ajalinshi, *Shureim*, shine yaron wanda Sa'ada a matsayinta na uwar yarinyar da kuma yaron tayi k'ok'arin b'oye wannan laifin dan kar mutumcin yaranta ya zube a idon duniya, bata so 'yarta ta rasa kimarta ta 'ya mace, ta d'auki zunubin da hannu bibbiyu ta d'ora akanta, tayi mana k'arya duk dan ta kare mutuncinsu, ta yaudari mijinta dan ta tseratar dasu a matsayinta na uwa, ta nuna mana zata iya yin komai akan 'ya'yanta, tabbas laifi ta aikata amma fa a dalilin soyayyar da take wa yaranta, muyi k'ok'ari mu fahimceta dan Allah, uwa takan iya yin komai ta kan iya tarar kowane bala'i saboda yaranta." Ajiyar zuciya tayi tace "Da wannan nake nema mata alfarma a wajenku dan Allah ku yafe mata, kuma iyayen yaran nan ne, ku kamalta da idan kune abun ya faru a idonku me zakuyi? Nasan ko baki abinda tayi ba zakuyi makamancin shi." Tirk'ashi! Yanzu abinda ya faru kenan da 'yarsu da kuma d'an su? Tambayar da suka ma kansu kenan? Sai dai Hajia ta gama sage musu gwiwa, ta gama dasu tunda tace k'addara, babu wanda ke kauce mata inda ta tashi fad'a masa, sannan ta k'ara d'auresu da tace tana nema mata alfarmarsu, uwa ce ita gare su sannan Ummy ta rik'e yaran kamar ita ta haifesu a cikinta, sun gamsu ba tayi haka bane dan ba ita ta haifeta ba, sai dai su ce kawai k'addarar da kuma sharrin shaid'an, bugu da k'ari ma abun ba yanzu ne ya faru ba, shekaru har biyar to wane fad'a zasuyi kuma da dama ya wuce suyi hak'urin? Cikin jinjina al'amarin Gambo ya kalli Hadiza ya kuma kalli lieutenant yace "Abinda ya shiga tsakaninku kenan har kuka samu sab'ani da matar da baku tab'a sab'awa ba?" Ajiyar zuciya lieutenant ya sauke yace "Gaskiya raina ya b'ace sosai, matata uwar yarana ta ha'ince ni har haka? Mtsss." Hadiza ma data gama sawa zuciyarta ruwan sanyi ta yanke hukunci taushe komai ta had'iye ya zama sakayyar da zata musu na kula da yaranta da sukayi ta kalle shi tace "Abban Ammar, dan Allah muna nema mata alfarma kayi hak'uri ka dawo da ita, tayi hakane saboda 'ya'yanka, idan zaka nutsu kayi tunani zaka fahimci da a lokacin kowa yasan abinda ya faru, kayi tunanin irin abinda zai faru marar kyau, sannan kayi duba da shekarun da kuka d'auka ba tare da kun samu sab'ani irin haka ba, kayi hak'uri dan Allah, mu ma wallahi mun yafe babu komai, Allah ya yafe mana baki d'aya." Gambo ne ya kalle shi yace "Ku daina bashi hak'uri ma dan Allah, yanzu zai tura dreba ya d'aukota ya dawo da ita." Wani kallon ban son iskanci lieutenant ya mishi, shi ma hararanshi yayi yace "Allah sai kayi ko baka so, ba dan ma raini ba matar taka ta shekaru zaka yarda ta bar gidanta a wannan lokacin, to ina kake so taje? Ko kunya abun ba zai baka ba ace ta tafi gidansu, da yaranku da jikoki ku tsaya kuna abu kamar yara." Had'e fuska yayi yace "Gambo, kayi shiru da bakinka kafin ranka ya b'ace." Shi ma ba alamar wasa yace "Ya b'ace d'in mana, an fad'a maka ina jin tsoro ne." Tasowa lieutenant yana fad'in "Zan tosheka kuwa yaro." Da sauri Gambo ya tashi yayi baya yana dariya yana cewa "Ni ne yaron? Ni kake kalla ka kira ni yaro? Haba." Hajia ce tace "Karka tab'a min auta wallahi, inba haka ba ranka zai b'ace." Dawowa Lieutenant yayi ya zauna yana murmushi, Hadiza kam banda k'yalk'yata dariya ba abinda take, komawa yayi shi ma ya zauna yana dariya, Hajia ce tace "Dole zaka tura a d'aukota, kuma ba dreba kad'ai nake so ba, har da kai ma zaka tafi." Kallonta yayi yace "Haj..." Bata barshi ya k'arasa ba tace "Bana son jin wata magana, abinda ka mata zaisa taji kamar ba a bakin komai take a wurinka ba, ba zan lamunci haka ba gaskiya, matar data k'arar da shekarun rayuwarta a tare damu, ta maka biyayya ni kuma ta min bauta, haka kawai yau ka wulak'anta ta." Cikin marairaicewa yace "Shikenan Hajia zan tafi, amma ki min uzuri dan Allah har zuwa gobe, wallahi yau ina da muhimmin aiki a gaba sosai." Fuska a d'aure tace "Shikenan, kaje Allah ya bada sa'a." Da farin ciki ya amsa da "Ameen nagode." Tashi yayi ya kallesu yace "Sai anjima." Husseina ve tace "Allah ya tsare." Sada ya fita Gambo ma yace zai fita ya dawo kafin Hadiza ta shiga d'aki ta samu Hamna, kwance ta same ta gefenta farantin kankana amma da alama bata sha ba, zaune tayi tana kallonta tace "Tashi zaune zamuyi magana." Cikin muryar kuka tace "Dan Allah Mama in akan maganar nan ne kawai ki barta, ba zan iya ba wallahi." Ajiyar zuciya ta sauke tace "Tashi Hamna, c'est très important." Tashi tayi ta zauna tana ci gaba da share hawaye kuma wasu na bin wasu, kallon basira ta mata kallon fahimta tace "Hamna, me yasa kika ce ba zaki iya auren Ammar ba?" Da sauri tace "Mama je ne peut pas, ba zan iya auren mijin yer uwata ba, kuma ni bana son shi ko kad'an." Saida ta karanci yanayinta kafin tace "Corrections, mijin yer uwarki data rasu zaki ce, sannan Hamna zaki iya aurenshi ko da baki son shi, kinsan me yasa?" Da ido ta kalleta hakan yasa tace "Saboda shine uban d'anki Shureim." Da fari zaro ido tayi tana kallonta a firgice, sai kuma ta fad'a kan k'afafunta tana kuka tace "Mama kiyi hak'uri ki yafe min dan Allah, wallahi ba laifi na bane shine ya tirsasa ni, Mama bana manta tunatarwarki a kanmu kullum, dan Allah kiyi hak'uri." D'agota tana share mata hawaye tana ji kamar tayi kukan ita ma tace "Karki sani kuka Hamna, na riga dana yafe miki har da shi ma, bana so ki karyar min da zuciya kuma." Sassautan kukan tayi sai ita data d'ora da cewa "Hamna a gani na ki amince da auren shi, sai nake gani kamar ba zaki samu wanda zai dace dake ba kamar shi, sannan Hamna duk wanda zai fito neman aurenki yanzu ya zama dole a sanar dashi kina da yaro, kina ganin zai amince ya aureki duk yanda yake son ki? Ba lallai bane gaskiya a wannan yanayin da ake ciki, amma kinga shi ba zai k'yamace ki ba, zai rik'e ki kuma ya rik'e d'anku hankali kwance." Girgiza kai tayi tace "Mama zan samu amma ba dai Ammar ba, mutumin daya rabani da mutumci ne yaushe zan iya rayuwar aure dashi? Kuma shi ma fa kinji abinda yace yana da wacce yake so, to me zaisa na tusa kaina gare shi." Murmushi Mama tayi tace "Wallahi baya da wata wacce yake so Hamna, kawai ya fad'a ne saboda kinsan shi ba rainin wayo yake so ba, nasan yanzu yana can yana bala'i kin kalle shi kince baki son shi." Kallonta Hamna tayi tace "Mama kawai ko bar maganarshi, ni idan ma ban samu mijin aure ba zan zauna na ci gaba da kulawa da yara na." Da sauri tace "To ba gashi ba, Hamna kina son yaran nan sosai kuma kin k'i yarda kowa ya kama miki kula dasu, indai kina son ki ci gaba da rayuwa da su dole ki auri mahaifinsu, amma ba zan takura miki ba ki zauna kiyi tunani sosai, duk abinda kika yanke ki kira ni ki fad'a min." Tashi tayi zata fita tace "Mama ina zaki je." Juyowa tayi tace "Zan je gida na dawo na d'auki Ahmad." Fkta tayi inda Hamna ta shiga d'aukar kankanarta da d'aya d'aya tana sha tana kuma tunanin abinda Mama ta fad'a, lallai indai zata rayu da yaran da ko kukansu bata so dole ta bi shawarar Mama, amma kuma Ammar? Kai! Tana cikin wannan tunani wayarta ta shiga k'ara, d'auka tayi ta ga ko suna babu a lambar, d'auka tayi suka gaisa kafin ta tambaya wake magana, nan ya fad'a mata sunanshi tace bata gane ba, dan haka yace ta bashi izini ya zo zai ta ganshi ido da ido, burinta na son samun wanda ya dace yasa ta amince da ya zo anjima. *Tsautsayi* Bayan sallah isha'i ta gama shirinta cikin doguwar rigar shadda, duk da ba tayi kwalliya ba amma tayi kyau, wayarta ya kira ya shida mata ya zo, ko da ta aje wayar Imam ya shigo yana kuka wai Shureim ya dake shi, jawo shi tayi tana lallab'a shi ta bashi wayarta tace "Ka je kayi kallon abinda ka fi so karka bawa kowa, kuma zan ga Shureim d'in saiya gane kurensa." Cikin jin dad'i ya karb'a ya fita, ita kuma saida ta shafa turare sannan ta d'auki gyale ta yafa tasa takalmi ta fito, su Zeinabu ta samu a falo ta fad'a musu tayi bak'o a waje zata shigo dashi ciki, fatan alkairi suka mata ta fice. Tana fita ta shiga mamakin wanda ta gani, kusa da salon d'inta yake nan take ganinshi zaune a wata fada, da mamaki tace "Kai ne?" Murmushi yayi "Kin gane ni ashe? Na d'auka yanzu ma saina kwatanta miki." D'an murmushi tayi tace "Na gane ka mana." Gyara tsayuwa yayi yace "To ya kike?" "Lafiya lau, mu shiga ciki ko, ba'a barinmu tsayawa kan hanya." Gabanshi ne yaji ya fad'i sosai, tambaya ya wa kanshi to me ya kai na shiga ciki? Shi fa ba wata babbar magana bace ta kawo shi wajenta. Murmushin yak'e ya mata yace "Amma kafin nan mu gaisa ki san suna na, in ya so sai mu shiga ko." "Amma ai duk zamu iya yi a ciki." Ta fad'a fuskarta a d'an had'e, kallonta yayi yace "Hakane, amma in d'an jin tsoro." Wani irin kallo ta masa tace "Tsoron me kuma?" Cikin rashin gaskiya yace "Eh to, kin gane? Kawai dai, gidan na ku ne, nasan mutanen cikinshi, akwai abokaina dayawa." Wani kallo ta masa zatayi magana Imam ya fito daga cikin gidan da gudu yana kuka, tana ganinshi ta durk'usa ta rik'eshi tana fad'in "Imam me ye? Waya tab'a ka?" Kafin yayi magana Shureim ya fito da wayarta a hannu ya zo ya tsaya yana fad'in "Aunty wai dan na ce ya bani nayi jeux (game) shine ya k'i." Ranta a b'ace ta kalle shi tace "Shine ka fizga da k'arfi?" Mik'ewa tayi tsaye ta kamo kunnenshi ta kwad'a masa mari tana fad'in "Shine zaka saka min yaro kuka? Dan ubanka ban hana ka tab'a min su? Wallahi ka sake karb'ar min a waya a hannun sai na ci ubanka a garin nan." 😂 *Hamna kin taro match fa, da kin duba bayanki kafin ki fad'i haka.* *Ammar* da saida ya kusa kawowa gida motarsa ta tsaya, makanikenshi ya kira shi kuma ya k'araso k'asa saboda tafiyar ma na da anfani ga lafiya, tunda ya hangeta ya ganeta, k'ara hassala yayi dama a tafashe ya fita daga gidan, har yanzu yana nanata kalmar data fad'a ta *ina da saurayi*, ya rasa dalilin da yasa Hamna ta soka mishi wannan iskancin, a gaban iyayensu tace tana da saurayi kuma bata son auren shi. Sannan yazu ya dawo ya tarar da ita da saurayi a k'ofar gida tana hukunta masa yaro, wannan wace irin uk'uba ce? Bayan ta gaura masa mari kuma ta bishi da zagi, zagin ma ubanshi kawai take zaga, wato dan ta ga wani d'an iska a gabanta shine zata tsaya tana zaginshi, tunda dai ta zagi yaronshi ai da shi take. Amma ba damuwa zaiyi maganin saurayin kafin ita, shi daya zauna yana kallo yana jin dad'i tana zagar masa yaro amma bai hanata ba, dan baisan darajar 'ya'ya ba saboda bai da su shi, da azama ya k'araso wajen ta bayansu ba tare da sun san da zuwanshi ba, saida ya tsaya da kyau ya toge sosai yasa k'afarsa ta dama a gaban k'afafun saurayin nan da ko sunanshi Hamna bata sani ba bare ta fad'a mana ya kwashi k'afafunsa. Sai ji tayi kawai abu ya fad'i k'asa pamm, da sauri ta saki Shureim ta juya ta kalli ikon Rabb, bawan Allah bai san me ya faru ba, baisan wane shaid'anin bane a cikin shaid'anun, abinda ya sani kawai shine a cikin aljannun ma wannan gagararre ne, duk yanda akayi ko dai a gidansa ne suke tsaye ko kuma sun taka masa yara basu sani ba, amma wannan kwasa da aka masa ko jirgin sama yana shaida maka zai tashi ya d'aga ka daga kan k'afafunka bare kuma bil'adama. Yana shirin bud'e idonshi daga k'asar da fuskarshi ta daduma yaji an tokara masa gwiwar k'afa a baya an hana shi tashi, bai yarda yayi gamo ba saida yaji an figi hannunshi ta baya anyi ciri dashi, yana jin sautin k'arar gotawar k'ashin shi sanda aka karya hannunshi, azaba ce tasa shi sakin k'arfinshi ya daka uwar ihu. Yana jin k'ararshi ya sake cije leb'e yana fad'in "Au! Zaka iya ihu ashe." Tsakiyar kanshi ya dafe ya rik'e hab'arshi da d'aya hannu da niyyar kawai ya juyar masa da wuya, an jima uban kowa bai mutu ba, Hamna data shiga firgici na abinda zai aikata bata san sanda ta rumgume shi ta baya ba ta rik'e hannayenshi gam ta fashe da kuka tana fad'in "Dan Allah Ammar sake shi baiyi komai ba, dan Allah karka kashe shi ka rufa mana asiri." K'arfin tartsatsin da yaji kamar k'arfin dake cikin wutar lantarki ne, ba wai tsayawa ba daga masifa, hatta numfashin shi ma ta kusa sawa ya bar jikinsa, har jikinshi ma ya shida ita ta musamman ce, sannan dokinshi ma ya tabbatar da yana kewar mace, dan a take sak'on yaje ya kuma haifar da sakamako mai kyau. Sakinshi yayi tare da mik'ewa tsaye yana kallon mutumin, shi fa ko fuskarshi ba bai gani ba, tsabar fitina ce kawai da neman wanda za'a mutu tare, sai lokacin ta sake shi tana k'ok'arin su kalli juna sai kawai ya taka da sauri yaja hannun Imam da Shureim wanda dukansu sukayi shiru da kukansu suna kallon babbar harka, cikin gida ya shige dasu. Cikin jin kunya ta kalleshi ya tashi zaune yana karkad'e k'asa a fuskarshi yana furzar data bakinshi, a hankali cikin taushin murya tace "Dan Allah kayi hak'uri kaji, kayi hak'uri da abinda ya maka, yayana ne." Shi dai da har yanzu bai gama gane komai ba ga hannunshi dake zugin bala'i na karaya ko kallonta baiyi ba, ko da taga haka ta mik'e ta shige gida da gudu da niyyar yau saita kawo k'arshen wannan bura'ubar da yake mata a gidan nan. Shima yana ganin shigewarta ya fashe da kuka na gasken gaske yana birkid'awa yana rik'e hannunshi da yake jin kamar zai cire ya barshi, gashi ba zai iya tuk'a motar ba bare ya kai kanshi wajen magani, baida nutsuwar da zai iya kiran wani ya zo ya d'aukeshi, mai gadin gidan ne yaji kukan babban mutum a waje ya fito da gudu, da taimakonshi ko da ya duba hannun yace karaya ce, tsaf ya mishi magani yasa mishi magani yanata addua'r Allah ya sawak'e, saida aka gama yace mi shi "Amma ba kaine bak'on da ka zo wajen Hajia Hanne (Inji shi)?" "A'a." Ya fad'a yana tashi tsaye, shima tsaye ya mik'e yace "Amma garin yaya ka karya hannu haka? Gashi kuma banga alamar hatsari ba." Huyowa yayi ya kalleshi, hatsari? Hatsari ma yake cewa baiga alama ba, bayan abinda ya faru yafi karon babbar mota muni, juyawa yayi ya ci gaba da tafiya a hankali yana d'an sosa bayanshi inda ya daka mishi gwiwa, motar ya bud'a ya shiga ya tayar ya fara janta a hankali yana tuk'i da hannu d'aya, sai dai ya ci alhwashin ko ma uban waye wannan yayan nata wallahi saiya tara masa yaran nan na unguwarsu yan zaman kashe wando sun ciro masa jijiyar dake sadar da ji da ganinshi. *Allah yaba mai rabo sa'a.* *Ko da* ta shiga da masifa a falon ta same shi yana wa Shureim bala'i yana fad'in "Akan banzar waya zaka zauna ana zagin ubanka a gaban k'aton banza, me yasa baka buga wayar a k'asa ba ta b'are? Duk duniya idan ka cire ni ubanka da uwarka da kuma yan uwanka ban yarda ka d'auki raini a hannun kowa ba, kaji na fad'a maka." Girgiza kai Shureim ya shiga yi yana sako da hawaye, tana bayanshi a hassale tace "Wannan har d'ab'ia ce kake jin kana koya masa to?" Juyowa yayi ya kalleta, kallon jin haushi da zan iya miki komai, ganin bai tanka mata ba yasa tace "... *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:38 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _67_ Ammar me ye matsalarka da samari na? Akan wane dalili ne kullum ka ganni da saurayi saika wulak'anta ni a gabanshi ko kuma ka muzantashi? Me yasa? Ka fad'a min idan ba haka ba yau ni da kai a gidan nan wallahi sai dai duk mu babbake." Da fari da kallonta yake yana tunanin hannun da idan ya bigeta dashi zata fi jin zafi, amma data ce wai duk su babbake sai ta bashi dariya, dariya ya shiga yi hankali kwance wanda hakan ya sake hassalata cikin d'aga murya ta kalli Hajia dake zaune tana kallonsu kamar tv tace "Hajia ki mana tsakani da bawan Allahn nan ya daina shiga tsakani na da samari na, tunda dai ba zamansa nake ba kuma ba aurenshi ne akai na da zai addabe ni ba." A hankali Hajia ta d'an dafe kanta dan ciwon kai taji suna neman sanya mata, lallai da taso a had'a aurensu, amma yanzu tunaninta shine yanda wannan yara zasu zauna in aka aurar dasu, lallai gaskiyar Junaid ne gidan nan zai iya kamawa da wuta, ganin Hajia ma ta k'yalesu saita k'ara jin haushi tace "To Allah idan na sake tsayawa da saurayi ka min iskanci Ammar saina soke ka da wuk'a." Hajia ta kalla tace "A matsayinki na kakarshi Hajia ki fara nema masa magani, dan wallahi ya gama kwancewa." Sama da k'asa ta bishi da harara ta giftashi zata wuce d'akinta, cikin salon da ka rantse bashi yayi maganar ba yace "Nan gaba ma wuyansu zan fara takawa, kin k'waci kanki da rumgumar da kika min, amma kika sake gigin zagar min yaro sai jini ya fita a bakinki, dan abu d'aya dana lura dashi shine baki k'aunarshi, to ni ina son kayana ehee." Tab'e baki tayi tace "Akan me zan k'aunace? Wannan d'in?" Ta fad'a tana nuna Shureim, gyara tsayuwarsa yayi yace "Me yasa baka son shi? Shi ba d'a bane?" Kawai dan ta b'ata masa rai tace "Saboda bai min ba." Gabanta fad'uwa yake saboda kallon da yake mata, murya k'asa k'asa yace "Me yasa bai miki ba?" Da sauri Hajia dan ta tsayar da maganar tace "Hamna wuce d'akinki bana son tashin hankali." Har ta fara takawa sai kuma ta tsaya ta kalleshi, cikin gadara da isa da rashin tsoron abinda zai biyo baya tace "Saboda da kai na same shi." Wucewa tayi ta barshi tsaye, had'e labb'anshi yayi yana lasarsu, har ga Allah baisan ta yanda zai fara fad'awa yarinyar baya son ya ga ana nuna masa k'iyayya ba, musamman ma daga mutane masu mahimmanci a gare shi, saboda bata son shine yasa ma bata k'aunar d'an data haifa dashi, to wace irin k'iyayya ce take masa?Wani shu'umin murmushi yayi dan har ya tsara abinda zai rama shi ma, juyawa yayi ya nufi d'akin Ummy sai Hajia da tace masa "Bata nan." Tsayawa yayi ya juyo yana kallon agogon hannunshi, shi dai duk yau banga Ummy a asibiti ba, to kuma in bata gida tana ina kenan? Saida ya zo kusan Hajiar yace "Ina taje a wannan daren?" Tsakiyar idonshi ta kalla yanda ba kowa da falon zaiji ba tace "Tana arlit yanzu, amma gobe Abbanka zai je ya taho da ita." "Arlit kuma?" Bata bashi amsa ba sai kallonshi da tayi kawai, sunkuyawa yayi kamar zai fad'a kanta shima cikin rad'a yace "Hajia lafiya? Yaushe ta tafi ? Me yasa kuma ban sani ba?" Kafeshi tayi da ido kawai hakan yasa yace "Dama ta fad'a min Abba na mata wasu abubuwada ni kaina fa bana jin dad'insu? Ko dai korarta yayi?" Saida ta d'aga kafad'a tace "Kusan haka." "Kusan haka." Ya fad'a yana jinjina kai, fita yayi daga falon yana tunanin abunyi. Kamar kullum yaran sun tafi b'angarenshi suna ta wasarsu, Ameera yaja a jikinsa ya kwantar da ita saman k'irjinta yana lallab'a yana shafata, da wani abun ya d'auki hankalinta ta mik'e zata tashi saiya mayar da ita kwance, tun suna haka har ta gaji bacci ya d'auketa, ko da ya lek'a fuskarta yayi dariya yana d'an cike leb'enshi yace "Da kanki zaki zo na hukuntaki kan tsiwar da kika min." Ci gaba yayi da kallon yaran saida suka gaji suka ga dare yayi sannan Ameer ya kama hannun Imam yace "Abba gida zamu tafi, Imam bacci zaiyi." Aje Ameera yayi kan kujera yace "Muje na raka ku to." "Ameera fa?" Ya fad'a yana kallon Ameera dake bacci, saida ya kama hannunsu suka nufi k'ofar fita yace "Tayi bacci mana." Ameer ne yace "Abba Ummy fa ba zatayi bacci ba idan bata nan, tare suke kwana akan gadonta." Murmushi yayi yace "Sai ka ce ta zo ta d'auke ta to." "To." Ya fad'a suna shiga b'angarensu, saida ya ga shigarsu falon kad'ai ya dawo, d'aukar Ameera yayi ya kaita d'akinshi ya shinfid'e ya dawo ya kashe wuta da tv ya kwanta kan kujera yana jiran zuwanta, ya sani ne dole ta zo dan zata iya hak'ura in cikin mazan ne amma banda Ameera, yarinyar data tab'a yanke hannu da reza wajen k'in ji, ita kuka yarinyar ma kuka aka rasa wa ya yanke d'in. Ko da suka shiga ta k'are musu kallo tace "Ina Ameera?" Ameee ne yace "Abba yace kije ki d'aukota tayi bacci." Sak'e tayi tana kallonshi, Abba kuma? Lallai ma ai ita d'in ba sakarya bace, bayan ihu da rashin kunyar data masa zata yarda taje su had'u, ai sai dai in a cikin mutane suka had'e, kallonsu tayi tace "Ku je ku kwanta to." Wucewa sukayi kowa ya kwanta a inda yake kwantawa, hannayensu duk suka d'aga tare da ita sukayi addu'a kafin suka shafa a jikinsu, tana hangensu har bacci ya d'aukesu cikin nutsuwa, tashi tayi ta k'ara gyara musu kwanciyar ta sumbaci kowane, dawowa tayi kan gadonta ta d'auki wayarta, lambarshi ta kira lambar data kasa gogeta a wayar kuma ko sak'on gaisuwa babu mai aika ma wani. Sanda kiran ya shigo wayarshi saida ya ji tsinkewar gaba dan abu ne da baya faruwa ko ya jima bai faru ba, saida ya k'ara gyara kwanciyarshi ya lumshe ido sannan ya d'auka, cikin muryar da ko a bacci ya tashi takan zama kamar ruwan d'umin dake wartsakar da gajiyarsa, muryar da ko hayaniya take masa yana iya tsayawa ya saurare ta, murya ce da ko halin rashin lafiya yake yasan zata iya zama wani muhimmin maganin da zai taimaka masa wajen warkewa, lumshe ido yayi sanda tace masa "Hello." Ba tare daya bud'a ido ba yace "Ya akayi?" Saida ta sake tausasa murya tace "Ameera, tayi bacci ne?" "Umm." Ya fad'a k'asan mak'oshi, marairaicewa tayi tace "Dan Allah ka taimaka ka kawo min ita, ba zan iya bacci nesa da ita ba." Wani murmushi yayi yace "Wai ke mahaukaciyar ina ce?" Cikin zazzak'ar murya kamar mai rera masa wak'a tace "Ta gidanku mana." D'orawa yayi da "Inba haukanki ba wa ke son 'ya'ya kuma ya k'i ubansu?" Jujjuya idonta tayi dan ta fahimci zai ja maganar da tsayi ne ita kuma bata da wannan lokacin, a hankali tace "Malam ni dai taimaka ka kawo min yarinta, yarana ina son su saboda suna da nutsuwa hankali da sanin ya kamata." Jim yayi yana fassara kowace kalma data fad'a, iska ya furzar yace "Ba damuwa, kankana, idan akwai abun rubutu kusa dake ki d'auka ki rubuta, wallahi akwai ranar da zata zo ba wai ki min rashin kunya ba, sautin muryata ma idan kika ji sai kin nemi wurin b'uya." Bushewa tayi da dariya tace "Ammar, amma zazzab'i na damunka ko?" Shi kanshi murmushi yayi mai ciwo irin yanda wai Hamna ce ke soka masa iskanci irin na yaran zamani, cikin sigar gargad'i yace "Amman dai kinsan waye Ammar ko? Sannan kinsan kalar na wa iskancin, muje zuwa tunda haka kike so." Gyara kwanciyarshi yayi yace "Abu d'aya nake so dake shine, ki janye wannan kalmar da kika fad'a a kaina da kuma yaro na." Cikin k'aguwa tace "Zaka kawo min 'yata ko sai na zo da kaina?" Murmushi kawai yayi kamar yana gabanta bai tanka mata ba, hakan yasa ta kashe wayar ta aje kan gado, wayar ya bi da kallo kafin ya aje ta gefe, har ya shiga tunanin duniya kuma Hamna da taji ba zata iya hak'ura ba ta sake kiranshi, ko da ya ga kiran kashe wa yayi amma saida ta k'ara maidowa, sake kashewa yayi ta k'ara kira a karo na uku, a k'ufule ya d'auka yana fad'in "In mayya ce ke ki ci kanki kankana, wannan wace irin masifa ce ba zaki barni nayi bacci ba, ke dai da gani zakiyi jarabar tsiya." Ido ta zaro tace "Wace irin jaraba kuma malam? Daga kira ta waya." Cikin masifa yace "To uwar me zan miki? Me yasa ba zaki kira saurayin nan naki ba mai zubi da figaggar tantabara kiyi hira dashi ba." Cikin sanyin murya tace "Ammar me yasa ka daki d'an mutane? Wallahi ko sunanshi ban sani ba daga had'uwar farko ka same shi ka narka kamar kai ka haife shi, kasan dai baka kyauta ba kuma wallahi Allah zai saka masa." Tintserewa yayi da dariya yace "Ni ma Allah zai saka min na shiga hurumina da yayi, kuma ina so na nuna miki irin mazan da kike soyayya dasu duk babu wanda zai iya rik'e ki." Cike da gatsali tace "Sai kai kenan ko me?" Murmushi yayi yace "Ni ai na fad'a miki goma kamar ki ma zan rik'e su, bare ke dana yi wa wanka na saka miki d'an wando da hannu na." Kamar sub'utar baki sai cewa tayi "Haba ko da nace, ashe tun ina yarinya ka gama lalata ni." Dariya yayi kamar yana gabanta yace "Da yanzu shekararki nawa da mutuwa to?" Cikin rashin fahimta tace "Ban gane ba?" Saida ya d'aga sauti yanda zata ji da kyau yace "Ina nufin a yanzun ma ba zaki iya d'aukata ba, ina ga tun a waccen lokacin ne? Hamna waccen ma maleji nayi kinji." Kamar zata fashe da kuka tace "Ammar Allahya isa, kuma karka manta ka ma yarinyata addu'a ka shafa mata, mugu kawai." Wata sanyayyar dariya ya bushe da ita yana kallon wayar data kashe, tashi yayi ya shiga d'aki ya samu Ameera, addu'a ya mata kamar yanda ya nema kuma yake wa yaran, shafa mata yayi tare da komawa d'akin marigayiya wanda har yanzu kayanta kenan ya kwanta, zanin rufar yaja ya rufe duka har kanshi. Abune daya zamar masa jiki yanzu duk zafin da ake saiya rufe kanshi da zanin saboda k'amshin turaren Amna da yake jikin zanin, da iskan turaren ya fara barin zanin saiya sake d'auka ya zazzaga, hakan na samar masa da nutsuwa sosai. K'arfe *03:47* na dare Ameera ta farka, madarar da take sha babu ita kusanta kuma babu kowa a tare da ita, tasowa tayi ta fito falon ma babu kowa, a cikin fridge yana aje madarar saboda ya san suna buk'ata yaran, amma sai ba tayi tunanin bud'awa ba ta d'auka, haka kuma bata tsaya nemansa ba saita tunkari k'ofa, uwarta kawai take son gani taji dad'i, dama bai rufe k'ofar ba saboda tunanin Hamna zata zo, ko da taji ta bud'e saita fita ta nufi b'angaren, amma matsalar shine k'ofar shiga falon Hajia a rufe take, jijjigawa ta shiga yi amma shiru ga kukan tsintsaye dake tsoratar da ita, sulalewa tayi ta zauna manne a jikin k'ofar, a hankali ta saki fitsarin da take ji a wurin. Ganin dai babu motsin kowa kuma babu mai shirin zuwa saita fara rera kuka,Tsawon wannan lokaci Haka tayi shi zaune ita kad'ai tana kuka tana son yin bacci, kiraye kirayen sallah yasa mai gadi ya fito dan yin alwala, amma duk kai da kawon da yayi Allah bai nuna masa ita ba saboda akwao duhu ma. Firgigit ta farka kamar wacce tayi mummunan mafarki, ko da ta bud'a ido juyawa tayi inda yarinyar ke kwanciya bata ganta ba, ganin lokacin sallah ma ya kusa saita ta tashi ta shiga ban d'aki tayi alwala ta dawo, har ta bud'a wajen kayanta da niyyar sake na jikinta na bacci, a hankali a hankali sai take jin kamar sautin kuka k'asa k'asa, shiru tayi tana saurarawa har dai ta fito daga d'akin, a lokacin da Ameera ta farka ta k'ara fashewa da kuka mai gadi ya ganta, matsowa yayi yana dubawa da kyau, cikin tsoron ko dai ba yarinyar bace yace "Wacece nan?" D'aga kanta tayi ta kalleshi fuskarta duk tayi jina jina da hawaye da bacci a idonta, cike da mamaki ya sake cewa "Hajia k'arama ce? Me kike yi anan?" Cikin kuka da maganarta bata ko fita tace tace "Wajen Ummy zani." Sai lokacin ya saki jikinshi ya matso sosai ya fara buga k'ofar, daidai lokacin Hamna ta fito taji ana buga k'ofar, take a wurin ta sawa ranta Ammar ya dawo da Ameera ta tashi a bacci kenan, sam mantawa tayi da riga da wandon dake jikinta, wando iya gwiwa yake na sojawa ne sai rigarshi bak'a mai k'ananan hannu amma ba sirara ba, da sauri ta shiga saukowa zata nufi k'ofar sai ga Labaran shima ya fito tare da yaranshi maza ya iza k'eyarsu gaba zuwa masallaci, karo suka ci sai Kamal da shima ya fito daga nashi d'akin daga sama, rage saurinta tayi ta kalli Labaran da yace "Ina zaki tafi kike sauri haka?" Cikin girmamawa tace "Naji ana buga k'ofa ne." "Nan?" Ya fad'a yana nuna k'ofar, da "Eh." Ta bashi amsa tana kallo ya hanzarta zuwa ya bud'e, mai gadi ya gani tare da Ameera a hannunshi, Hamna na tsinkayarsu bata bari wani cikinsu yayi magana ba ta daka a guje ta finciko Ameera ta rumgume a jikinta, kallon fuskarta take tana share mata hawayen da har sun fara bushewa, kallon mai gadi tayi tace "Ina Abbanta yake? Daga ina ka d'aukota?" "Wallahi nima anan na ganta ita kad'ai tana kuka, tace wajenki zata tafi." Cike da tausayi ta kalleta tace "Abbanki ne ya kawo ki?" Girgiza mata kai tayi hakan yasa tace "To yana ina?" Cikin shahsek'ar kuka tace "Ban ganshi ba." "To ya akayi kika taho nan Ameera?" Ta fad'a cikin yanayin tashin hankali, murya k'asa k'asa tace "Ban ga Abba na ba kuma ban ganki ba, shine na taho wurinki kuma k'ofar ta k'i bud'ewa." Cikin d'aga murya kamar za tayi kuka tace "Tun yaushe Ameera? Kin jima anan d'in?" Yarinya da babu hankali sai tace "Tun da daddare." Zaro ido tayi da matuk'ar tsoro ta sako da hawayen tausayi tace "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, yanzu Ammar nan ya bar min ke kikayi kwana." Labaran ne yace "To shiga da ita ci..." Bai gama fad'a ba ya ga Hamna ta aje Ameera ta wuce da sauri ta nufi b'angaren Ammar, Kamal ne ya kalli Labaran yace "Tonton muje muyi sallah, gobarar nan ubangiji ne kawai zai iya kashe ta." Wucewa sukayi sallah har da mai gadi, tana zuwa da k'arfi ta bud'a k'ofar falon ta shiga, ba tsayawa komai ta tunkari k'ofar d'akin baccinshi, tana daf da kaiwa shi kuma ya bud'a ya fito zai tafi masallaci shima da doguwar riga, kamar wata zakanyar da aka cinyewa ya'yanta suna had'a ido taga shine kawai tasa k'arfinta da hannayenta ta tura shi baya da k'arfi, k'ofar d'akin ya kaiwa karo yana kallonta da mahaukacin mamakin lafiyarta. Cikin kuka kamar an ce mata Ameera rasuwa tayi da d'aga tace "Ammar me yasa zaka min haka? Me yasa zaka bar min yarinya ta kwana a tsakar gida ita kad'ai kamar wata marar gata, me yasa baka kira ni na zo na d'auketa ba in kai ba zaka iya kai min ita ba? Haka kawai ka maidata kamar wata *marainiya*." Cikin rashin fahimtar inda kalamanta suka dosa ya matso kusanta yace "Wace yarinyar wai? Ameera kike nufi? Amm..." "Amma me?" Ta fad'a da k'arfi, d'orawa tayi da "Saida na kiraka nace ka kawo min ita, ko ban kira ka ba? Kasan ba zaka iya kula da ita ba shine ka k'i kawo min ita tsabar mugunta, kuma ai kasan ba wajenka suke kwana ba, amma tsabar fitina da nema na da magana ka rik'eta wajenka." Sake matsowa yayi kusanta yace "Ke yi k'asa da muryarki, d'anki ne ni da zaki zauna kina min fad'a, dan fa yana asuba ne bana masifa a irin wannan lokacin." "To kayi mana, na ce kayi, ni ita nake nema da kai." Duk tayi maganar ne tana turashi baya da k'arfinta, saida ta ga ya dangane da bango ta nuna shi da yatsanta mai d'auke da doguwar afaifa da bak'in lalle tace "Ya zama na k'arshe kenan da zaka k'ara k'ok'arin rabani da yarana, wannan ba samari bane da zanyi shiru idan ka shiga tsakani na dasu, akan 'ya'yana saina dafaka da ranka kuma na shanye romon." Ido ya zaro tare da bud'e baki irin firgicin nan cike da shak'iyanci yace "Mayya ce ke dama? Yaushe kika fara cin naman mutane?" Sama da k'asa ta daddala masa harara tace "Tun ranar da bak'in bakinka ya rairaye min k'iba ta." Juyawa tayi zata fita yace "Ki nemi abinda ya ramar dake kankana, amma ba bakina ba, kuma nasan kema kinsan ko a ina matsalar take." Tsayawa tayi ta juyo tace "Babban matsalata a rayuwa kai ne Ammar." Sake juyawa tayi zata fita abinda zata iya cewa bai tab'a faruwa ba, indai kaga jikinshi a hannunta to mugunta ce zai mata, amma sai gashi ya rik'e hannunta kuma ba da k'arfi ba, hasalima yatsunta ne ya rik'e yana mammatsa su a hankali a hankali, matsowa yayi kusanta saida ya tsaya gabanta yana kallon fuskarta, tayi shiru alamar abun ya ratsata, babu wani yanayi a tare da fuskarta na bak'in ciki ko b'acin rai, fuskarta dai kamar tana bacci yanayin nutsuwa sosai. Yana kallon fuskarta cikin yanayin fahimta shima yace "Hamna kina son yaran nan sosai, rabaki dasu abune da ba zaki ji dad'inshi ba, amma me yasa kika k'i amince da maganar iyayenmu na son had'a aurenmu?" Da sauri ta kafe tsakiyar idonshi da kallo, kasa d'aukewa tayi kuma ba tace komai ba, shima ba tare daya rusunar da idonsa ba duk da hakan kuwa na galabaitar dashi yace "Hamna kina da girma da mahimmanci a zuciyata fiye da tunaninki, ni mai iya mallaka miki yarana ne har abada sun zama naki, amma matsalar d'aya ita ce idan kika auri wani, ba fa lallai ya barki tare da su ba kamar yanda kike so, kuma na tabbata iyayenmu ma abinda sukayi la'akari dashi kenan suka so had'a aurenmu, amma da yake mahaukaciya ce ke lamba d'aya sai kika kawo wani mai suffar yan tsaki wai shi kike so." Har yanzu idonta na kanshi cikin taushin murya tace "Nice mahaukaciyar?" Saida ya kawar da kansa yace "Eh mana." A hankali ta zame hannunta daga na shi tana fad'in "Ni da kai bamu dace ba Ammar, ba zamu iya zama a inuwa d'aya ba." Murmushi yayi yace "Tsakaninki da Allah idan na baki umarni ba zaki bi ba?" Saida ta dafa girarta sama tace "Me zai hana ni bi, zan bi mana idan bai sab'awa Allah ba." K'wayar idonta ya kalla yace "Tsakaninki da Allah baki jin komai a kaina?" K'asa tayi da nata idon tace "Kamar me fa?" D'an ja baya yayi yace "Ranar dana samu hatsari sai gashi naga tsoro fargaba da tausayi a idonki, ranar da zamu bar garin nan tare da margayiya kin d'aga murya akanta, sannan duk da abinda na miki baki iya d'aga muryarki kowa yaji ba, hasala dake ake ta rufa rufa, an fasa aurenki sau uku amma babu wanda kika damu dan an fasa shi, wannan duk menene *kan..ka...na*." Yanda yaja sunan kankanar yau sai taji sunan ya mata dad'i a kunne, amma dan karta saduda a gabansa sai kawai ta yamutsa fuska tace "Kai kuma a yanda ka fahimci abun kenan? Gaskiya kana buk'atar ganin likita." Rab'ashi tayi zata wuce ya bi bayanta da kallo, rintse idonshi yayi dan ba zai yarda alwalarsa ta karye ba yace "Kina mantawa da ni likitan zuciya ne ko?" Tsayawa tayi ta juyo ta kalleshi, murmushi tayi ba tace komai ba dan haka yace "Shekaru na b'ata ina wannan karatun, matakan kare kai daga kamuwa da cuta har zuwa yanda zaka mu'amulanci marar lafiyarka duk a karance nayi shi, karki d'auka haka kawai na zama tantiri a gidan nan Hamna, komai da nake yi ina sane nake yinshi, duk abinda zanyi ina yi ne dan ya tsayawa kowa a rai yayi nishad'i da zulumi, lokuta dayawa kuma har ayi dariya, taya kike ganin ba zan karanci kowa da halin da yake ciki ba." Takawa yayi ido rufe saida ya tabbatar ya kai gareta kafin ya bud'a ido ya wuce ta bai tsaya ba, fita yayi ya wuce masallaci ya barta tsaye, da kallo ta bishi tana takawa a hankali ta koma wajen Ameera, ya daki zuciyarta sosai amma taji haushinta kanta data yarda ya ganota, ko da yake ma ai k'arya yake yi bata jin komai a game dashi, abinda ya fad'a tayi kawai yayi dogaro da su ne dan ya kunyata ta, dan haka kawai ta share al'amarinshi. *Ko da* ya dawo daga masallaci ya kira wayar Ummy, batan ta d'auka sun gaisa yake ce mata "Ummy Abbanmu na nan tafe zai zo d'aukarki, amma kinsan me?" Daga b'angarenta ta amsa da "A'a saika fad'a." Gyara tsayuwa yayi yace "... *Allah yasa ba zugaki zaiyi ba uwarmu.* *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:38 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _68_ "Wai Ummy Abbana mijinki na shekaru barkatai, yau dan kin masa wani d'an laifi shine yana kallonki kika fice a gidan nan bai tsayar dake ba, Ummy ba wannan yafi damuna ba kamar yanda wai saida Hajia ta lallab'a sa tace ya dawo dake, wai Ummy kinga kuwa yanda take rok'onshi, humm ai ni abun ya mugun b'ata min rai wallahi, ji nake ina ma ace nine wallahi...hmmm shikenan dai Ummy sai anjima, zuciyata ma zafi take zan je nasha magani." Ko da ya gama fad'a ya kashe kiran, Ummy da tunda ya fara magana take dariya ta riga data hango manufarshi, murmushi tayi tana kallon wayar tace "Ja'irin yaro nasan me kake nufi, zanyi yanda kake so dan nima raina ya b'ace." Shima ko da suka gama wayar wanka ya shiga ya fito ya shirya cikin farar shadda, fita yayi hankali kwance yana istigfari da hailala a bakinshi har ya isa mak'abarta, a gaban k'abarin yake durk'ushe, kallon k'abarin yake inda abubuwa da dama ne ke zuwa mishi a kanshi, na farko akwai wa'azantarwa a game da lamarin mutuwa, sannan rayuwarshi da ita tarihi ya kafu wanda babu abinda zai iya goge shi, addu'a ya shiga kwaranya mata kamar saukar ruwan sama, ya d'auki tsawon lokaci kafin ya shiga gabatar da addu'a ta duka musulmin dake kwance, tare da addua'r Allah ya kyautata nasu k'arshen yasa mu cika da imani, awa d'aya da rabi ya d'auka a mak'abartar kafin ya juya ya tafi cike da kewar ma'abociya aminci da salamarshi. Gida ya koma ya cire kayan nan ya saka wando iya gwiwa ya kwanta abinshi a falo. Da safe d'aya daga cikin wanda suke zama tare yaje har gida ganinshi daya fad'a masa abinda ya faru dashi jiya, a k'ofar gida suke tsaye yana jajanta masa, shi dai kunya da takaici basu barshi ya fad'i abinda ya faru ba, saida abokin yayi shirin tafiyarshi sai yace "In tambayeka mana abokina?" "Uhum! Ina ji." Cewar abokin yana kallonshi, gyara tsayuwa yayi yace "Dan Allah kasan yayan yarinyar nan Hamna?" Kallonshi yayi yace "Hamna? Wacece hakanan?" D'an tsaki yayi yace "Yarinyar nan mai salon mana ta kusan fada." "Oho, na gane, wane daga cikin yayanta? Kasan fa yar gidansu Jibril ce." "Yayanta ne shi?" Cikin rashin tabbas yace "Eh to ban sani ba gaskiya, kasan yawa ne da mutanen." "To kasan Ammar?" Shi ma ya fad'i hakane saboda yaji sunan daga bakin Hamna sanda tace ka k'aleshi Ammar, cikin rashin kulawa yace "Ina jin sunanshi dai a gari." "To baka san wani wanda ya san shi ba?" Cikin kallon rashin fahimta yace "Akwai Jibril, d'an uwansa ne, amma me yasa kake nemanshi?" "Ba ruwanka, kayi k'ok'ari ka samo min da hoton shi kawai." Yanda yayi maganar zaka san ba lafiya ba dan haka yace "Ka fad'amin mana me ke faruwa?" "Ba komai, in zaka samo min ka samo min, in kuma ba zaka iya ba ka bani lambar Jibril d'in." Cikin damuwa yace "Haka kawai shi ba mace ba na zauna ina neman hoton fuskarshi, ba zan iya ba gaskiya, d'auki lambar Jibril d'in kai saika kirashi da kanka." "Bani." Ya fad'a yana bud'a sécurité na wayarshi dan d'aukar lambar, yana juyawa ya tafi shi kuma yayi kiran Jibril, faran faran suka gaisa cikin sakin fuska, saida Jibril yace ban gane ba sannan yace "Eh ba zaka gani ne ba, abokin Ammar ne ni, dan Allah inba damuwa fotonshi nake so ka turo min, shi ya k'i turo min ne dana tambaye shi." Ko alama Jibril baiyi mamaki ba ko tunanin wani abu daban, abinda ya sani kawai shine watak'ila Ammar zai raina masa hankali da fuskokinsu biyu shi da Amar, dan haka sai yace "Ba damuwa, yana son yi maka iskanci kenan ka rasa gane shi." Da farin ciki yace "Yawwa nagode sosai." "Ba komai." Ya fad'a shima sukayi sallama, lambarsa ya shigar a wayarsa kafin ya tura masa hoton Ammar d'in na ranar d'aurin aurensu, ko da yaga hoton ya k'are masa kallo yace "Duk yanda akayi wannan soja ne, dan dukanshi ma bana wasa bane, amma zan rama an dad'e ba'a yi sama aka durmiyo k'asa ba." *Da yamma* Abba suka shiga garin kai tsaye gidan k'anwar mahaifiyarta *Ardayi* suka wuce dan yasan can zata nufa, matar akwai karamci da sanin takamata, dan kamar yanda a gida suke ganin laifin lieutenant ita kuma laifin Ummy take gani, dan Ummy bata b'oye mata komai ba, yanzu ma da suka zo cewa tayi bata ji dad'i ba daya k'yaleta ta zauna gidan har ta gasu, faran faran suka gaisa ta kuma jadadda mishi hak'uri da kanta tare da cewa yarinta ce😂, lieutenant kanshi saida yayi dariya, ciki ta shiga ta kira Ummy ita kuma ta shiga had'a mata kayanta dan su wuce duk sanda suke so. Tun kafin ta k'araso inda yake zaune kan kujera ta basar ta had'e fuska irin ba wasan nan, tana zuwa ko zaune ba tayi ba ta tara masa hannu, 😂 (Allah gamu gare ka) d'aga kai yayi ya kalleta da mamaki, mayar da kanshi yayi k'asa bai tanka mata ba, cikin jujjuya baki tace "Kai nake jira." D'aga kai ya sake yi ya kalleta, ba alamar wasa shi ma yace "Baki iya sallama bane?" Saida ta turo baki tace "Ina wuni." "Ba wannan na tambayeki ba ai." Kallonshi tayi sai kuma ta juya baya ta rik'e k'ugu ta sake mik'a hannunta tace "Ka bani na juya na koma ina da abun yi a ciki." Kallon nutsuwa ya mata yace "Me zan baki wai? Kin bani ajiya ne?" Juyowa tayi da mamaki tace "Ban gane me zaka bani ba? Takarda ta mana." Da sauri ya kalli idonta yace "Kinga Sa'ada ba wasa na zo muyi ba, ki d'auko kayanki ki wuce mu tafi, komai dare ina so mu bar garin nan." Wani yamutsa fuska tayi tana kallonshi tace "Ai ba haka mukayi da kai ba, ko ka manta?" Kallonta yayi sai kawai ta ma bashi dariya ganin har wani girgiza take wai ita rashin mutumci take so ayi, mik'ewa yayi ya tsaya gabanta yana k'are mata kallo yace "Jaraba kike so muyi Sa'ada?" Saida ta rage girman idonta tace "Eh, ai gidanmu ne nan ina da masu tsaya min." Ba alamar annuri yace "To ni kuma kinga a gidan naku zan kakkarya ki kuma a gode min akan haka, amma bana so a k'ara miki wani dukan bayan wanda zan miki, dan haka in bala'in kike ji muje gida sai ayi." Matsawa tayi baya tana fad'in "A'a me zai kaini gidanku, ni na zo gidanmu kenan ai da kake gani na nan, da kaga na fita to..." Shiru tayi tana k'yabta ido dan bakinta yake kallo kamar jiran yaji me zata fad'a yake, saida ya kawar da kanshi yace "Ki d'auko jakarki mu tafi, in kuma ba zaki tafi ba ki gaya min." Saida ta juya d'an k'aramin bakinta mai d'an tsayi kafin tace "Eh." Da kyau ya kalleta yace "Eh me?" Saida taja baya sosai ta saita k'afafunta k'ofar shiga cikin d'akin Ardayi sannan tace "Ba zan tafi ba." Da sauri ta k'arasa shigewa ciki tana ma kanta dariya, da kallo ya bita yace "Eh lallai yarinta ce kamar yanda Hajia suka fad'a." Fita yayi ya samu dreba suka k'arasa wani masauki mai kyau a garin suka yada zango anan, dan ya lura wannan bikon mai tsada ne na gaske, watak'ila saiya salwantar da wasu zinariya kafin ta yarda su koma, tunda dai ba zai yarda yayi tafiyar banza ba, uwa uba kuma umarnin gwamnatinshi ce dole a cika ko ba'a so. Saida akayi sallah magrib yayi wanka yana kwance ya d'auki wayarshi ya tura mata gajeran sak'o kamar haka "Uwar Ammar ce quoi t'on problème? Qu'est ce que tu veux?" Sanda ta samu sak'on murmushi ta saki ta mayar masa da harufa hud'u tace "Rien." Shi ma maido mata yayi da "In dai hakane to ki yarda mu koma gobe." Maido masa tayi da "Indai hakane saika yarda zaka hau rak'umi a garinmu." Zaro ido yayi yana k'ara nanata karantawa, maida mata yayi da "Amma ai na hau lokacin aurenmu, me zaisa yanzu na hau da girma na haka kawai." Cikin basarwa tace "Shikenan sai ka koma inda ka fito kai kad'ai." Ba alamar wasa a amon muryarshi yace "Kinsan Allah, wallahi tare dake zan koma, bari ganin fa ina lallab'a ki sa'a ce kika ci." Wata dariya tayi kafin ta maido da " *Sa'ada, Sa'adatu sa'ar mata, ko bakiyi kyau ba kinyi sa'a*, ka daina fad'in sa'a a gabana sunanta gare ni." Iko sai Rabba, da mamakin wannan sabon canjin dan shi dai bai santa da shi ba yace "Nima fa har yanzu ban huce kan abinda kikayi ba, dan kin samu na zo shine sai kin waina ni." Kafin ta maido ya kirata a wayar dan ya tabbatar mata ta shirya gobe zasu koma, ko da ta d'auka tace "An zo wurin, ai dama an fad'a min ba da son ranka ka zo ba saboda ba so na kake ba dama, shiyasa nake so kawai ka bani takardata tunda banda mahimmanci a wurinka." Cike da mamaki yace "Sa'ada ni? Ni ne kike fad'awa haka?" "To ai gaskiya ce." Ta fad'a tana juya baki kamar a gabansa, cike da kokonto yace "Anya kuwa Sa'a baki yi waya da babban d'anki ba? Dan naga irin fitinarsa ke kike min yau d'in nan." Kai tsaye tace "D'ana ba fitananne bane gaskiya kawai yake fad'a." "Shikenan." Ya fad'a yana d'orawa da "Yanzu fad'a min abu d'aya, zaki shirya ko kuma ba zaki shirya ba, dan ba zan zauna ina lallab'aki ba sai kace wasu yara masu shirin aure." Cikin muryar shagwab'a da kuka tace "Eh mana kace haka, idan kana tare dani sai ka nuna min mun girma mun tsufa muna da yara da jikoki, amma idan ka shiga d'aya d'akin saika d'anyance ka zama yaro kana kinibibi..." Duk da ta kai k'arshen kalmar amma saida ta rufe baki, rarraba ido ta shiga yi tana saurarenshi yana fad'in "Ade nine kinibabben? Ba damuwa karki je d'in ki ci gaba da zama anan." Kashe wayar yayi ya aje gefe, shi kad'ai kamar wanda aka tab'a saiya fashe da dariya kuma, wai kinibibi? Shi ne yau ake ma rigima, ko Zeituna dake yarinya ai yanzu ta daina tunda ta haifi nata yaran, in kaga rigimarta yanzu ita ma tana son wani abu shi kuma yaga yanzu ya wuce wannan ajin, to fa haka zasu kwana tana botsare masa yana tarota tana baud'ewa. A gida kuma rabon ayi zamu ce Amar na kan hanyarshi ta dawowa gida saida ya shigo cikin kwanar gidan wasu samari biyu suka sha gabansa, tsayawa yayi ya bud'e mota ya fito, tunda dai suka ga fuskar wanda suka gani a waya aka kuma biyasu kan su jigata shi sai kawai suka mame shi da duka, su bakwai ne dan haka babu yanda ya iya dasu, dan bak'in ciki kuwa shi ma saida suka masa tsinanniyar karaya a hannu, abunka ga unguwar masu hali babu hayaniya mota ko moto ma sai jefi jefi suke wucewa, saida suka ga ya daina motsi suka barshi nan ba tare da sun raba shi da komai na sa ba sai su da suka d'ora masa takarda a kan jikinshi. A k'alla mota uku ta wuce amma babu wanda ya kula dashi, Junaid ne kad'ai da yaga motarshi ce anan ya tsaya da niyyar tuntub'arshi yaji lafiya, ya shiga tashin hankali sosai ganinshi a kwance kamar ba ma kama bace babu rai kam, gigicewa yayi ya rasa ta ina zai fara, sai yayi bakin titi da gudu kuma ya dawo yayi hanyar gidan kamar ya k'arasa, yayi haka har sau hud'u kafin daga bisani ya fara kiciniyar janshi zuwa mota, a lokacin kad'ai takardar data fad'i ma ya kula da ita, da sauri ya d'auka tunaninshi abune mai mahimmanci, saida ya bud'a ya karanta rubutu kamar haka " _Duk wanda ya min kankara sai nayi masa na itace, baka dake ni ka karya min hannu akan banzar k'anwarka ba, to ka dafata ka cinye kai kafin nan muyi jinya tare, banza dak'ik'i mai k'walwar kifi."_ Da sauri ya zura takardarshi ya ci gaba da janshi har ya sa shi motarshi ya fizga ya bar erea, da suka tafi ganin yan uwa ne da yallab'ansu suka karb'eshi da gaggawa, dan su duk da sun san Amar amma tashin farko ma sun d'auka Ammar d'in ne, cikin ikon Allah suka samo shi dan dama k'ananun raunika ne sai karyar hannu da suman da yayi, saida aka bawa Junaid kyakyawan labari kad'ai ya samu nutsuwar kiran d'an biyun Amar d'in. 😂😂😂 Wallahi yana gida kwance yana kallo ana lallasa d'an uwanshi sakamakon masifarshi, da Junaid ya fad'a masa cikin tsananin damuwa da d'an uwanshi yace yana zuwa, bai d'auki lokaci mai tsayi ba ya isa ya same su, har ga Allah Junaid bai nuna masa takardar nan ba dalilinshi kuwa shine, in dai ya gani to baisan ina rigimar zata tsaya ba, a sanin daya ma Amar ba mutum ne mai rigima ba, shi fa da Ammar d'in ne to ko shakka ba zaiyi ba, amma Amar har yanzu abun na bashi mamaki, duk tambayar daya masa sai dai yace ba komai ko ban sani ba ko uhum, haka ya d'auki Amar yace ai sai dai su koma gida, ya zaiyi inba zuba ido ba, yana kallo ya labta Amar a bayanshi ya fito dashi har waje kuma yana k'orafi wai zai karya masa baya k'aton wofi. Da suka dawo gida ma zasu kaishi b'angarenshi ce ma Junaid yayi "D'ora min shi a baya." Saida yayi dariya yace "Kamar wani yaron goye, dan Allah ka barshi zai tafi da k'afarshi." Amar ma cikin yanayin jigata yace "Zan iya tafiya, nagode." Kallon fuskarsa yayi ya masa gwalo yace "Ka daku fa, wai waya dake ka haka kana tsaye kana kallo kuma?" Saida suka fara takawa suna rik'e dashi yace "To ni ina na sani, rufeni kawai sukayi kamar Allah ne ya aikosu." Ammar ne yace "To me ka musu? Fad'a kake yi dama a waje?" Murmushin k'arfin hali yayi yace "Fad'a dai Ammar? Haba dama dai kaine ai ba za ayi mamaki ba, na sani yanzu ma wani ja tsokana shine ya sauke akai na da tunanin ni ne kai, ai kasan ba yau aka saba haka ba, kankana ma nasha cutuwa a hannunta idan ta tashi zuwa d'aukar fansa." Shiru Ammar yayi, tunanin kalaman Amar yake yi, tabbas fa maganarsa gaskiya ce, to idan fa hakane? Amma waye ya zo dukanshi ya daki d'an uwanshi? Wane mai k'arar kwana ne wannan? Har suka kai b'angarenshi bai iya tunawa ba, to ai abun dayawa😂 ba zai iya cewa gashi ba, shi ya sani a dangi ma ana jin haushinsa bare kuma waje, duk da dai wanda fad'a ya tab'a had'asu dashi na akai ga jiki ba yawa ne dasu ba, shi ma kuma shi ne ke saurin kai hannu maimakon cacar baki, wanda kuma ya dank'arawa magana da zagi da yan k'ananun abubuwa basu da adadi, Jano kuma da yayi sanadiyar shigarshi gidan maza shi bai ma san a ina ake ba yanzu, dan tunda aka kama shi ya rufe babinshi ya shiga wata sabgar, sai wanda ya daka suna tare da marigayiya Amna, sa kuma wannan na jiya shima, to cikinsu kuwa akwai wanda ya daki d'an uwansa. Saida suka shiga suka zaunar dashi Farisa da Umaimah hankali tashe suke tsaya kansu suna tambayar me ya faru dashi? Babu wanda ya basu amsa sai Ammar daya kalli Farisa yace "Ku samo mishi abinci ya ci yasha magani. "To." Ta fad'a tana nufa madafa, Junaid ma fita yayi yaje ya sanar da iyayensu, dukansu suka rukuto suka taho da mamakin abinda ya fad'a musu da kuma jimami. Ko da Junaid ya fita ya kalli Amar yace "Dan ubanka fad'a min wa kayi fad'a dashi?" "Allah babu kowa, to wai me zai kaini fad'a kamar marar aikin yi ko yaro k'arami." Ko da su Hajia suka shigo sun samu yana fad'in "To inba wani abu kayi ba wa zai maka wannan dukan har da karya maka hannu." Cikin tashin hankali suka jajata masa suna tambayar ba'asi, maganar dai d'aya ce bai san komai ba kawai an rufe shi da duka ne, sai lokacin Junaid ya fara lalaba aljijunshi yana fad'in "Bari kuga abinda na gani kusa da inda na same shi kwance, abun yafi kama da d'aukar fansa." Firo da takardar yayi ya mik'a ma Ammar, daki daki ya shiga kallon kowace kalma yana hardaceta a kanshi, kowa ya zuba masa ido suji me zai ce sai ji sukayi ya gunduma wata ashar yana fad'in "Kuturun uban cen, ni? Yanzu nine wannan yaron ya ma tarko dan ya dake ni? Shine har da wata tsinanniyar wasik'a yana kirana da dak'ik'i, kankana kuma ita ce banzar? Banza fa, bayan yace min mai k'walwar kifi, ah lallai." Mik'ewa yayi yana jefar da takardar zai fita Junaid ya rik'oshi yana fad'in "Ina zaka je Ammar? Ka wa Allah da manzonsa abun ya tsaya iya haka?" Kallonshi yayi yana murmushi yace "Haba dai kaima fad'a kawai kake, k'anan na wa su masa wannan dukan sannan ya kira kankana da banza, ni kuma dak'ik'i mai k'walwar kifi kuma ka ce na k'yale, to miye anfani na kenan inhar zan iya yin shiru kan wannan cin zarafin." Zai wuce ya sake rik'eshi sai Hajia da tace "Ammar dan Allah dan uwarka Sa'ada ka k'yaleshi koma wanene, kaga dai abinda ya faru yanzu bala'in ya fad'a kan d'an uwanka, ita fa fitina kwance take mu ne ke tashinta." Hajia ya kalla yace "Dan Allah Hajia ki cire bakinki a maganar nan, abu d'aya da nake so dake shine ki kira tonton colonel ki fad'a masa yau zanyi kisan kai ya tanadar min wuri a gidan maza, mazan ma k'arti manyan yan ta'adda." Husseina ce tace "Subhanallah, mun shiga uku mu kam, Ammar kisan kai?" Ko kallonta baiyi ba ya fincike a hannun Junaid ya tunkari fita, karo suka ci da kankana da yara suka fad'a mata iyayen na b'angaren tonton Amar, bata san hawa ba bata san sauka ba kawai yace "Yar banza mai shegen farin jini, to yau dai gashi banzan lusarin saurayin naki da kika kunyata iyayenki akan shi shine ya turo miki sak'o yake kiranki da banza, wai banzar k'anwata na dafa ki na cinye." Ita dai da bata fahimci komai ba wucewa tayi ta gaishe da Amar tana masa ya jiki, dawowa yayi yana kallonta ya ci gaba da zazzaga masifa wai duk ita taja, ko kallonshi ma ba tayi bare ta kula shi haka kowa ma yaja baki yayi shiru, saida ya kalli kowa yace "Eh mana ga d'an iska mahaukaci na magana, dole kowa ma yayi shiru, to ni na tafi sai kunje gani na a gidan yari." Kamar zai tashi sama ya nufi k'ofar fita cikin rashin kunya Umaimah tace "... *Insha Allah zanyi k'ok'ari nayi wata page d'in anjima amma fa idan kunyi comment, ku shirya kowa ya kawo goron d'aurin auren fitinannu na.* *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:38 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _69_ "Yanzu dama akan ka ne aka dakar min mijina? Dan Allah yah Ammar wace irin rayuwa ce wannan kai da jan masifa shi da shan duka? Ya kamata fa ace kasan ka girma amma irin haka bai kamata ba, yanzu gashi baisan hawa ba bare sauka kawai an sauke mishi kwandon rashin mutumci, gaskiya dai akwai alhaki wallahi Allah ma ba zai barka haka ba, haba mutum sai jaraba kawai k..." Kamar saukar aradu kowa yaji Hamna ta daka mata tsaw da cewa "Ke." Juyawa tayi ta kalleta suka shiga kallon kallo kafin ta nuna mata shi tace "Umaimah tsaranki ne shi da kike fad'a masa haka? Saboda an daki d'an uwansa wanda na tabbata baki fi shi jin zafin a zuciyarshi ba, ki tambayi shi yah Amar d'in kiji kafin ki ci masa albasa, shin yana jin haushin d'an uwansa kan abinda ya faru yanzun?" Cikin rashin mutumci tace "To ke kuma a wa? Dake nake bare ki sa min bakinki? Ki bari shi da nayi dashi ya tanka min mana amma bake ba." Murmushi ta mata tace "To ai naga ba shi ne daidai ke ba, ni nan ni ce daidai da ke wallahi." Ammar dake kallon ikon Allah saiya bushe da dariya ya nemi kujera ya zauna yace "Buga min ita a k'asa kankana, yau saina cika miki gidan nan da kankana Allah kuwa." Kallonshi tayi ta dalla masa harara ta mayar da hankalinta kan Umaimah da tace "Kin tare masa saboda ke ce daidai dani? Ko kuma kin tare masa saboda shine uban d'anki?" Hajia da Husseina ne suke musu magana amma bata saurare su ba saida tace "Ki d'auka a yanda kika ga zai fi miki sauk'in d'auka akan ki, amma idan zan zab'ar miki sai nace barshi dan yana uban d'ana, ai kinsan saduwa ba k'arya bace, haka ma haihuwa ba wasa bace, ai ke wannan abubuwan biyu ne yasa kike tayar mana da jijiyar wuya saboda an tab'a mijinki, ke ga mai miji maji dad'in miji." Cikin shewa da tapa hannaye tace "Wuuuu! Alhamdulillah Ina da mijin da zan iya nunawa, kuma nagode Allah daya bani mijin da nake jin dad'in dashi, ke fa? Har yanzu gantali kike a titi har kin tsofe a gari babu mai so, sannan kaf yarana na haife su a k'ark'arshin inuwar aure, har nayi zamani na ban aje d'an dak..." Dan bai da kuzarin da zai tashi ne amma yayi niyyar marin fuskarta, dan haka kawai ya daka mata tsawa da cewa "Umaimah." Shiru tayi tana hararan Hamna wacce ita ma ke kallonta tana murmushi, cikin b'acin rai ya gyara zamanshi yana kallonta yace "Umaimah me yasa baki da hankali? Ta tsawarta miki ne saboda kina d'aga murya kan babba kuma d'an uwana da take da tabbacin ba zan ji dad'in abinda kika masa ba, yaushe zakiyi hankali ne wai?" Wani harare ta sake dalla ma Hamna tana turo baki gaba tana gunguni, ba tare daya daina kallon fuskarta ba yace "Ba tace ki tambaye ni ba? Me yasa baki tambaye ni ba? To bari ni na fad'a miki kiji da babban murya, wannan dukan da d'an uwana aka wa shi wallahi ba zan sake cin abincin gidan nan ba har sai ranar da idona suka ga cikakkiyar lafiyarsa, Umaimah ina farin ciki sosai da godiya ga Allah da dukan nan ya tsaya kaina, yanzu haka na yafewa wanda yasa aka dake nin, amma da d'an uwana ya daka har abada babu yafiya tsakani na da shi, dan haka wuce d'akinki bana son ganinki a wurin nan." A hassale ta kalleshi tace "Ni ce ma mai laifi kenan? Ba damuwa." Ta fad'a tana wucewa d'akinta, da harara ya bita cike da takaicin hallayarta yana fad'in "Inma da damuwar fa sai me." "Hahahahahahahahahahha, wuuuuuuuuuu, wayyo Allah na, Hajia kin gani ko?" Cewar Ammar kenan dake nufa kusan Hajia, nuna mata Hamna yayi yace "Allah Hajia yarinyar nan so na take, kiji fa yanda take fad'a dan an tab'a mata ni, wuuu! Gaskiya zamuyi kyau da aure." D'ora kanshi yayi kan kafad'ar Hajia cikin jin kunya yace "Dan Allah Hajia ki daure ki aura mata ni, kinji?" Me Hamna za tayi ba dariya ba, har ga Allah shirmenshi ko rashin kunyarshi suna bata haushi da takaici, amma na yau saiya bata dariya da yace wai ta daure ta aura mata shi, kallonta yayi ya kalli Hajia yace "Kin gani ko, na fad'a miki ai." Junaid ne yace "Yanzu ya maganar d'aukar fansar to? Ka hak'ura kenan?" Kallonshi Husseina tayi kallon ya kuma zaka tuno masa? Kallonshi yayi yace "Hak'uri fa? Ai wannan maganar ma bata taso ba yaro." Hanyar fita yayi Hajia ta fizgo hannun Hamna cikin rad'a tace "Ki wa Allah Hamna naga kamar ke d'in aljanunshi na sonki ki dakatar dashi, karya je ya kashe d'an mutane." Kallon Hajia tayi ta had'e fuska tace "Ni kuma Hajia? Rufa min asiri na mutu maza su binne ni, ba wani aljanu wallahi iskanci ne." Cikin rad'a tace "Amma dai kinsan zai iya ko?" Tunawa tayi da abinda ya faru jiya sai kawai tace "Gaskiya kuma." Turata Hajia tayi tace "Yi sauri to ce ya hak'ura ya dawo zan aura masa ke." Hararan Hajia tayi tace "Karku sa haukansa a kanku mana." Da sauri ta fita daga d'akin inda Amar ya kalli Hajia yace "Da zaku ji tawa Hajia sai nace ku aurar dasu, a yanda na fahimta duka suna son junansu." Murmushi Hajia tayi tace "Ba zasu yarda cikin sauk'i ba, amma zan musu na babba da yaro, in sun san wata ai basu san wata ba." Husseina ma dariya tayi tace "Gaskiya kam, musamman ma Hamna dai tafi taurin kai, amma shi na ga kamar k'uli yake duk inda ya fad'i gaba ne." Dariya Junaid yayi yace "Kai shi fa babu ruwansa, anya ma kuwa zai iya soyayya?" Zeituna da tunda suka gaishe da Amar bata sake cewa komai ba sai yanzu ne tace "Ai kuwa idan ya tashi yi zai baka mamaki, dan soyayya ma sai tafi wahalar dashi fiye da tunaninka." Kallonta yayi yana dariya yace "Tanti Ammar kuwa zai bari soyayya ta bashi wahala, ba fa zai iya rarrashi ko lallab'a ba bare kalaman soyayya." Amar ma dariya yayi yace "Ai daya fara ma zai ce ke dan ubanki dan kinga ina lallab'a ki." Ihun Hamna suka ji yasa suka dakatar da dariyarsu suka fita da sauri sai Amar kad'ai ke zaune yana girgiza kai, ko da suka fito a farfajiyar suka same su yayi k'arfa k'arfa ya shiga har d'akin mai gadi ya d'auko labceciyar wuk'arsa ko kuma takobi, Hamna ce tace mai gadi ya rufe k'ofa shine fa ya d'aga takobin yace bari ya fara ta kan mai gadin, dalilin kuwarta kenan, cikin tashin hankali da son kwantar da tarzomar kowa ya shiga bashi baki, anan Hajia tace "To kai da yanzu muke maganar aurenku kuma kana so ka shiga gidan yari, kasan dai ba zan aura maka jikata bayan ka fito daga gidan nan ba ko?" Husseina ce tace "Nima ban goyi da baya ba gaskiya, dan wata rana yar tamu zai kashe." Cikin nutsuwa Zeituna tace "Yah Ammar, ko ba komai dan Allah kayi tunanin yaranka mana, ko so kake ka mayar dasu marayu gaba da baya? Mahaifiyarsu ma Allah ya jikanta da rahama ba zata so ba hakan ba, ko ka manta ka tab'a fad'a min bata son rigimar da kake yi." Mik'awa mai gadi takobin yayi yace "Shikenan kun kashe wannan fitina, amma ku sani ban muku alk'awarin cewa idan na ganshi ba zan murd'e wuyan tsinanne ba." Kallon kallo suka shigayi suna ma kansu tambayar wannan ai shine an kashe maciji ba'a sare kansa ba, can kuma sai suka ji yace "Shiit, to ai kuma banga fuskarsa ba." Murmushi kowa ya saki na jin dad'i sai kuma ya kalli Hamna wacce tuni ta shiga rarraba ido dan tasan ba shakka zai koma kanta yace "Munafuka ke ai kin san shi, dan haka tare zamu fara yawo yanzu har sai kin nuna min shi." Hararanshi tayi tace "Saboda banda aikin yi? Ko kuma saboda kai na ya zare?" Da sauri Hajia tace "To kai yanzu ka yarda kayi ta yawo da matarka a gari kowa na kallo?" Kallon Hajia yayi yana murmushi yace "Mutane ai ba zasuyi kyau ba babu ido." "Kamar ya?" Cewar Junaid, kallonshi yayi yace "Idan na fara k'wak'ule maka ido zaka fahimta." Dariya yayi yana matsawa daga kusan shi, ta gabanta yabi ya shafi kumatunta yana fad'in "Allah ya gafarta miki duniyata, har nayi kewarta wallahi, da yanzu tana nan tana kuka tana cewa dan Allah yah Ammar ka tausaya min, karka fita ka zauna a gida, ni ka dake ni ma indai zaka huce." Da kallo su dai suka bishi har ya shige b'angarenshi, girgiza kai Hjia tayi tace "Allah ka shirya mana bawan nan naka, wannan idan muka k'ara samun wani kamar shi zamu mutu da ranmu." Dariya kowa yayi suka shiga ciki suna sauke ajiyar zuciya. *Da safe* ko da ya tashi da abun ya tashi a ranshi, sai yanzu ne yake asalin jin haushin abun sosai, ya zage shi ya zage abar son shi, a hakan ma wai bayan yasa an daddaka d'an uwanshi, a gaskiya ya gama shawowa dashi ba kad'an ba, wai shi ya kira da mai k'walwar kifi kuma dak'ik'i, shiryawa yayi ya fita bai tsaya ko ina ba sai alimentation, kifi ya siyo kifin ma babba ya kamo hanya ya dawo gida. Cikin madafa ya shiga dashi su Zeituna na ta k'ok'arin had'a abin kari, da kanshi ya d'auki babban faranti ya juye shi ciki ya d'auki wuk'a, suna kallon ikon Allah su dai ya cire kanshi tare da bud'e cikinshi, kwatta kwatta ya dinga k'arewa kan kifin kallo, basu ankara ba suka ji ya jefa wuk'ar ta bigi tagar dake kallon bayan gidan yana fad'in "Kaji haushi Ammar, ya had'aka da kifi kuma babu abinda kayi." Juyawa yayi zai fita ya ga duk suna kallonshi, nuna musu kifin yayi yace "Ku je ku duba kuga k'walwar tashi sai kuji dad'i tunda ya kamanta ni dashi." A hassale ya fita rai b'ace ya bar gidan gaba d'aya. *Tunda safe* lieutenant yaje dan su tafi, k'in fitowa tayi da farko amma tanti Ardayi tace ba za ayi wannan da ita ba, hannunta ta kamo ta damk'awa lieutenant sannan tace "To Allah ya kiyaye gaba, Allah ya kaiku lafiya sannan aci gaba da hak'uri." Saida ya duk'a har k'asa yace "Nagode Hajia, Allah ya k'ara girma da d'aukaka." Ko da suka fito waje ta fincike hannunta ta tafi da sauri ta shiga ta zauna inda dreba ya bud'e mata, rumgume hannaye tayi sai had'e rai take har suka d'auki hanya, babu wanda yace ma wani uffan har sukayi doguwar tafiya, lokaci lokaci ya kan kalleta sai yayi murmushi ya juya shima, wai hushi take bayan ita ce mai laifi, saida sukayi doguwar tafiya suka tsaya kan hanya wata k'aramar shago ya kalleta yace "In akwai abinda kike so ki fad'a min?" Shiru tayi kamar ba taji ba saida ya sake maimaitawa tace "Bana buk'atar komai." Kallonta yayi sannan ya kalli dreba yace "Mu tafi kawai." Suna hanya Hadiza ta kirata sosai suka gaisa kamar yanda suka saba kafin daga bisani suyi sallama, ko da yaji yasan da wa take magana dan haka ba tare daya kalleta ba yace "Mutuniyar kirki ce, dukansu sun yafe laifin da aka musu." Ita ma ba tare data kalleshi ba tace "Uwa ce ita, dole ta fahimci abinda yanda ya kamata." Murmushi yayi ya lumshe idonshi, shima fa yanzu baya jin haushinta kan abinda tayi, irin dai kawai shi namiji ne ba zai sauko da wuri ba, to kuma sai ita ma Ummyn ta hau sama, dan tun daga maganar nan bata k'ara cewa komai ba har suka isa garinsu. Hajia da kanta ta kira Hadiza ta sanar da ita maganar nan fa babu fashi, kawai su ma yaransu addu'a ta alkairi, haka ma Gambo ta kirashi ta fad'a mishi ya kuma ce wuk'a da nama na hannunta duk yanda tayi su addu'a da kuma yanda take so ne nasu, da kuma su Ummy suka dawo da dare take sanar dasu, duka dai kowa farin ciki ya nuna, amma da Ummy ta samu Hamna da maganar saita nuna ita fa bata so, duk k'ok'arin Ummy na son fahimtar da ita ta dage kan ita bata son auren Ammar, ba wai ba zata iya aurenshi bane kasancewarshi tsohon mijin yer uwarta yasa ba zata iya zama dashi ba ita, k'arshe dai haka Ummy ta rabu da ita dan karta takura ta har ta amince ba da son ranta ba. *Da sauri* *Abu* kamar da wasa sai magana ta girmama inda Hajia tace mishi za'a saka musu rana, amma fa duk abinda yasan ya ma Amna sanda zai aureta ita ma saiya mata shi, bai musa ba yace ya ji ya gani shi ai yaga abinda ya gani kuma yaji abinda yaji a na farkon ma, dan haka ribarshi ce bata wani ba. Tana ji sama sama aka saka ranar kawo kayan, haka duk take kallonsu da wutsiyar ido da gari ya waye taga suna shirin tarban bak'i, dan wannan karan tunda abun ya sauya daga dangin lieutenant zuwa na Ummy ga kuma abokan arzik'i da dangin Hadiza duk sun hallara, kamar yau ake d'aurin auren saboda yanda ake ta kayaniya ta ko ina. Da yamma aka shiga shigo da akwatina, tunda taji bud'a gabanta ya shiga fad'uwa tana tambayar kanta wai dama da gaske suke? Ammar? Ita? Lallai za'a mutu, tana sama ita dai tana jin gidan kamar zai tsage, a sama sama take jiyo maganganun mutane inda suke fad'in "Lallai wani hanin ga Allah baiwa ne, wani jinkirin kuma alkairi ne." Saida aka ci aka sud'e an kawo ashirin ta arzik'i an koma da arba'in ta arzik'i, dan Hajia ta bud'e bakin jakarta ta zazzagawa kud'i rashin mutumci, a cewarta *auren sabon shalelenta ne* sannan ba k'arya k'ok'arinshi ya birgeta duk da dai tasan kud'i sun sake zaunawa yanzu, amma shima ya rintse ido sosai wajen kashe yayan banki. Cikin k'ank'anin lokaci Hamna ta fara ganin statu d'in yan uwa har sun manna hotonta dana Ammar da kayan da kud'i da goro, statu d'in Sayyada (gaisuwa gare ki, sannunki da k'ok'ari da juriyar bayar da labarin yan uwan nan naki, wallahi kina k'ok'ari dasu😎 amma dan Allah karki fad'a ma cousine d'inki Hamna), d'aya hoton akwatina ne har goma ras an jerasu wasu na bin wasu, sai hoto na gaba inda aka bud'e dukansu kowa taf take da kaya har suna amai, sai na gaba d'aurin goro har guda hud'u da kud'i zube kan carpet yan jaka goma goma na million biyu, sai wata malet daban mai d'auke da tanfatsetsiyar sark'ar zinariya k'irar Agadez babu algus a cikin tare da awarwaro, wacce ita kad'ai ma kud'inta sun ishi mai rai rayuwa. Ba tace bata ji dad'i ba gaskiya, dan saida ta murmusa ma amma bata san na miye tayi ba, amma daga nan ta shiga tunanin yanda zasu yi rayuwa da mutumin nan, a gaskiya ba zata iya rayuwarshi ba ta sani, bata sani ba waye zai wahalar da wani cikin ita ko shi, gashi bata da ta cewa yanzu tunda sun riga da sun gama magana ba zata kunyata su ba, idan kuma iska ne jikinta dake hanata aure, to ta sani shi zai dakatar da auren inhar lokacin aurenta baiyi ba. Washe gari tana duba sak'onni WhatsApp d'inta ta samu sak'on Amie wacce rabonta da ita har ta manta, sak'o ne na neman tijara gajera kamar haka _"Burinki ya cika tunda gashi zaki auri mijin da yer uwarki ta bari bayan ta mutu."_ Ji tayi ba zata hak'ura ba ta maida mata da _"Na d'auka kin jima da fahimtar bana mu'amula da munafiki, amma bansan wace uwar kike nema tare dani ba."_ _"Ba ko d'aya, sai dai har yanzu ina tausaya ma yar uwarki, sannan da kike cewa baki zama da munafiki, ni ya kamata na fad'i haka, ko ke baki lura dana bar kulaki ba tunda nasan wacece ke ba."_ _"To kenan meya kaiki yi min magana kenan?"_ _"Dan na tayaki murna."_ Cewar Hamna _"Na ko gode."_ _"Mtsssss, anji haushin duniya, ki rasa wacce zaki ci amanar sai yar uwarki."_ Fita harkarta kawai tayi dan a ganinta ba zata b'ata lokaci kanta ba, sak'on Sayyada ta shiga wacce ke tambayarta ankon da zata fiddo musu, dariya kawai ta mata ita ma ta share ta, dan haka ta turo mata da "Karki d'aukeni yar iska mana Hamna, zan zo gidan da kaina naje na fito da anko." Maida mata tayi da _"Hakan shi yafi, amma duk abinda zakuyi tsakaninku ne ni bana ciki."_ Dariya ta mata ita ma tace _"Zaki sauko ne daga inda kika hau wallahi."_ _"Babu abinda zai sauko dani."_ Dariya ta sake mata tace _"Ai kuwa d'an uwana zai sauko dake da k'arfin cin tuwo."_ Maida mata tayi da _"Ke dashi duk baku da aikin yi."_ _"Ke ma zaki samu aikin yi idan aka d'aura, dan tunanin d'an uwana ma kad'ai ya ishe ki."_ _"😡."_ Shine abinda ta tura mata. A safiyar aka raba goro wani kamar zaiyi wanka dashi, sam kowa ya goyi da bayan a saka k'ank'anin lokaci, hutu aka saka na babbar sallah da za ayi na yan makaranta wanda duka *sati uku* ne ya rage, ai sai Ummy ta aje maganar aiki gefe ta fara shiga da fita tana gyara yar tilon yarta data rage mata mace, duk abinda ta wa margayiya shi take mata yanzun har da k'ari na sabbin sirrika, ita kanta Hamna wani abun in tasha sai jikinta yayi sanyi, wani in tasha tsikar jikinta ce zata dinga tashi, wani kuwa sai taji jikinta har rawa yake, turaren da take sawa a ruwa wurin wanka har gadonta ya kamu da k'amshin shi ma, ta samu gyaran fata tayi luwai luwai abinta tayi masara shar da ita, kullum kuwa tana sama d'akinta bata ganin ko falon Hajia bare rana, har yanzu kuma basu had'u da jarabun nata ba dan ba d'akin yake zuwa ba, dan danan kuwa sai gashi an gama shirye shiryen sallah an gama. _Zuma_ Idon zakara_ _Kanunfari_ _Garin rud'i_ Ka had'esu ka sha da nono ko madara. _Minanas_ _Hakk'in daka_ _Cukui_ _Zuma_ Saika had'esu kana sha da madarar shanu d'anya _Kankana_ _Gwanda_ _Abarba_ _Pomme (Apple)_ _Zuma_ _Madara peak_ Kayi jus na su kana sha. _Habba cokali 2_ _Garin rid'i cokali 3_ _Garin raihan cokali 4_ _Yayan zogale yanda kake buk'ata_ Ka zuba cikin dahuwar tantabaru mace da namiji. _Dabino_ _Nonon rak'umi_ _Hulba_ _Ayaba_ _Abarba_ _Zuma_ Ka tafasa nonon rak'umin idan ya huce saika juye shi cikin markad'add'sn dabino da ayaba da abarba ka zuba garin hulba kasha. *Kwana uku* daya rage kowace rana da shagalin dasu Sayyada suka gwangwaza, su da abokan Ammar sunyi shagali sosai ba kama hannun yaro, Hamna kam mulkinta take buga musu son ranta, har kamu akayi cikin gidan nan amma babu wanda ya ga k'afar amarya, anyi anyi ta shirya sai ma ta fashe da kuka dole aka k'yaleta, sai nan d'aki suka mata wanka turare, Ammar kam ko a jikinshi saida yaje gaban iyaye ya kwashi shokinshi ya duk'a suka fesa masa turare kafin ya bar wurin, wannan karan ma gabjejen sa ya aiko dashi ayi girkin biki tare da jus kamar za ayi wanka dashi. *Ranassss* Ya baje cikin shigar fararen kaya, lieutenant colonel da Gambo da Labaran duk shigar kala d'aya ce, su Amar Jibril da sauran dangi ma matasa kamarsu duk suna cikin fararen kaya, to anko ne da aka sa kowa yayi dan dole ko bai shirya ba, anan lieutenant ya bayar da auren yarsa inda Labaran ya karb'a wa d'ansa😂 (kune gayyar tsi...), daga k'arshe dai an d'aura auren *Hamna Harouna Suleymane Gaga* da *Ammar Hassan Suleymane Gaga* akan sadaki jaka hamsin mafi k'arancin dan albarkar auren. *Yanzu ciwon kaina zai k'aru ku taimaka min da panadol da paracétamol da doliprane a kusa.* *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:39 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _70_ *Biki yayi biki* ta bakin wani mawak'i, ba kid'a ba wak'a amma fa holewa ake, b'angarenshi ya sake tabka mishi gyara na rashin mutumci, haka kuma yana can ana gyara masa gidansa dan yace wannan ita ce abokiyar gwabzawa sai sun matsa daga kusan manya karsu kashe su basu shirya ba. Ita kanta Hamna k'awayenta sun mata bajinta sosai, dan har daga Niamey da Katsina wasu sun zo aurenta, taji dad'i sosai na ganinsu a kusa da ita a wannan lokaci. Ko da magriba tayi Ummy ta tsaya tsayin daka wajen gyara amaryarta kuma surukarta, wata mahaukaciyar doguwar riga ta tsadadden tissue aka saka mata, yaji d'inki sosai mai d'aukar ido da d'aukar hankali, tun daga sama zuwa hannaye har gwiwa a matse yake, amma daga k'asa sai aka bud'e sosai yayi tsatsaye har yana jan k'asa, kwalliya ta d'auka daga wajen wata k'awarta ta ban mamaki, kwalliya ce daidai da fuskarta inda aka d'ora komai kan muhallinsa, d'aurin d'an kwali kam kamar ba hannu ne yayi aikin ba, dama duk wani abin da zata saka saida Ummy ta turare shi har da pant da bras d'inta, sannan ita ma aka sa ta zauna kan kujerar turaren bayan an turare mata jiki, abubuwan da Ummy ta k'ara bata tasha ta ci taji tana neman yin amai, tana daf da fashewa da kuka tana fad'in "Wallahi Ummy amai zanyi, ya ishe ni haka dan Allah." Da sauri mai kwalliyar tace "Rufa min asiri Hamna karki zubo da hawaye a idon nan." Hararanta tayi tace "Dallah kwalliyar me?" Karb'a Ummy tayi tace "Shikenan to barshi haka, ai muna tare dake a gidan." Ummy zata fita daga d'akin wayarta tayi k'ara, ko da ta d'auka tace "Ango ya akayi?" Daga inda yake yace "Ummy kun shirya? Mota fa na nan tafe d'aukar kankana." Saida ta kalli Hamna dake ta had'e rai k'awarta na cewa ta dinga murmushi dan Allah sannan tace "Me ye na sauri Ammar? Kuma nan da can d'in zata shiga mota? To ai ko hannu aka sa sai a tura motar k'ofar gidan." "A'a Ummy sarauniya ce yau, bari mota zata kaita." "To shikenan." Ummy ta fad'a dan abar canzen, ta d'auka mota d'aya ce yake nufi da zata d'auki amaryar, amma abun mamaki da firgita tunanin mai rai sai jininin motoci suka ji, sanda aka fito ne suka ganewa kansu sarautar Allah, kai Umy ita dai a ganinta motocin nan bana abokanshi bane kad'ai kamar harda hayarsu akayi, mota ta bawa guda arba'in baya ta kusa kaiwa hamsin, to wace tsiyar zasuyi da su, in suka shiga ina za'a kaisu, to wata motar ma yanda ta zo haka ta juya ta koma bata d'auki ko sauro ba bare mutum. Bakin duniya, da suka kwashi matan mutane gudu na idon duniya suka dinga yi dasu, aa fa gudun ma a cikin tsari suke yin shi, dan babu motar data fita daga layin da suke, saida suka lula suka kai k'uryar ali d'an sofo sannan suka kutsi hanyar da saida ta sada su da zarya ta k'arshen k'ashe-sheshe, yawo kawai sukayi mutune tun ana jin dadi su dai har wani ya fara k'orafi saboda dare ya k'ara yi, sai lokacin kad'ai suka koma aka aje amarya aka shigar da ita gidan ta. Iyaye duk kanta suka taru inda suke mata nasiha kan hak'uri, saida kowa ya gama na shi Hajia da Husseina su dai suka fad'a mata ta zama mai d'auke kai daga lamarin bawan Allah nan, wannan taurin kai da fad'a masa magana kai tsaye ta kiyaye, tayi kamar yer uwarta har ta koma ga Allah ba'a tab'a jin ko sautin muryarsu ba da sunan tashin hankali, ita dai sauraronsu kawai take, amma ba zata iya abinda Amna tayi ba, wacce ta fad'a mata idan wani ya b'ata mishi rai saiya huce kanta ta hanyar darzata kan gado ko kuma ya mata wanka da ruwan sanyi ko sata cin abincin da batayi niyya ba, to ita yaushe zata iya da kwatirarsa? Ai ya kasheta ko ita ta kashe shi ne kawai. A sannu sannu aka watse aka barta ita kadai, zaune kan gado tana k'arewa d'akin kallo, saida ta gama tas sannan ta mayar da fuskarta cikin babban mayafinta tana kallon hannayenta masu ban lalle, Ammar? Ammar? Mahaukaci ne fa suka had'ata dashi. *Uwar Lalla kinji fa?* *Yana* saman hanya tare da Amar na tuk'i sai su Junaid a baya lieutenant ya kira shi, d'auka yayi lieutenant yace "Kana ina Ammar?" "Abba ina kan hanya." Cikin d'an jin kunya yace "Ka siye kaza ne?" Murmushi yayi yace "Abba duk angon dake son jin dad'i dolenshi ai ya siyo kaza." Su Amar kallonshi sukayi sai Abba da yace "To ka siyo guda biyu ina son d'aya nima." Tafin hannu yasa ya rufe fuska wai kunya yana fad'in "Lah Abba na wallahi ka bani kunya, kai ma kaza kake so? Kenan dai uwata zata mana k'ane." Had'e fuska yayi yace "Kai bana son iskanci, ita kad'ai ce mai k'wan haihuwa? To da uwarka nake ni." Ido ya zaro cike da shak'iyanci yace "Kai Abba na Ummy fa, kayi hak'uri dan Allah kaje wajen uwa Zeitu." "Ammar." Ya fad'a cikin muryar karsashi, a hankali yace "Na'am Abba." "To ka siyo ka kawo min, kuma dan ubanka da kai zamu je siyan bakin uwarta ka tunda kai ka zigeta har yanzu bata kula ni." Tintsirewa yayi da dariya yace "Abba na karka damu, ni d'in nan nine na rabaku kuma ni zan had'a ku, bari na siyo maka kaji manya guda uku, d'aya ta yau d'aya ta gobe d'aya ta jibi." Girgiza kai lieutenant yayi kawai ya kashe wayar, shi kam gyara zama yayi kamar mai shirin bacci yana fad'in "Abba ba dan karka karya min uwa ba ma ai da saina saka maka magani a kazar nan." Dariya suka saka inda Junaid yace "D'an iska dai baiji dad'i ba wallahi." "Inji uban wa?" Ya fad'a idonshi a rufe, Jibril ne yace "Inji shi mana." Wata k'arar ya fitar a bakinshi irin a banza kenan, Amar yace ma "Muje a siyowa Abba kaji, shi ma yau dad'i yake so yaji." Kallonshi Amar yayi yace "Yanzu kai banda abunka ina Hassan ina wannan abu na yara? Ai sai ku masu tafasashen jini." Bud'a ido yayi ya kalleshi sama da k'asa yace "Ko yanzu ka had'ashi da yarinya Allah zaka yi mamakin sakamakon da zai haifar." Su dai dariya suke har suka isa wajen madugu😋, tik'a tik'an kaji ya siya kafin suka wuce gida, da shigarsu suka samu lieutenant a waje, wuyan rigarshi ya shak'a yace "Sai mun je ka bata hak'uri, tunda ka hure mata kunne yanzu gaisuwarma sai dai kaji ta wani ce, ina kwana." Dariya yayi yace "Abba sake ni to ai ba guduwa zanyi ba." Sakinshi yayi suka shiga ciki gidan ya d'an fara yin shiru alamar kowa ya tafi bawa makwancinshi hakk'inshi, kai tsaye d'akin Ummy suka shige a tare. Ja sukayi suka tsaya ganin Ummy ta gama saka doguwar rigar bacci har k'asa tana d'aure gashinta da k'aramin mad'auri, kallonshi Ammar yayi yana dariya yace "Abba da alama ita ma hak'uri zaka bata, to gashi ni na tafi kafin na makance." Juyawa yayi yana ajiye leda d'aya lieutenant ya jawoshi, juyowa tayi ta kallesu tace "Ya zaku shigo haka babu sallama?" Juyawa tayi tana fad'in "Ko da yake ai kamar uba kamar d'ansa, ba mamaki kam." K'arasa shiga sukayi inda lieutenant ke fad'in "To miye a ciki dan bamuyi sallama ba, kai da kaya ai duk mallakar wuya ne." Kallonshi tayi fuska a had'e tace "Amma ai shi yaron mamallakina ne, ba shine ya mallake ni ba." Kallon juna sukayi da Ammar yace "Wannan shalelen Hajia ko bayan raina fa shi zai rik'eki." Ba alamar wasa tace "Shiyasa dama ka k'i bani takardata saboda kaga ka kusa mutuwa, kana so dole sai nayi maka wankan takaba." Gaba d'aya suka juya suka kalleshi yana dariya, zaune Ummy tayi bakin gadon tana kallonshi, saida ya gaji da kanshi yace "Ummy Abba na kike wa fatan mutuwa? To ai bai tsufa ba." Da hannu ta nuna masa tace "Ka duba da kyau ka gani, kwana nawa ne ya rage masa yayi ritaya (retraite)?" Murmushi yayi yace "Amma Ummy ai a wajen aiki ne zaiyi ritaya, a gida kuwa yana nan da k'ark'onshi." Lieutenant ta kalla tana d'an jujjuya baki tace "Zaku iya fita idan kun gama abinda ya kawo ku." Kallon juna suka sake yi sai yayi laushi sosai yace "Abba ni zan tafi fatan nasara, mata uku ne dama ke matuk'ar jigata ni a duniyar nan, ga d'ayar nan." Ya nuna Ummy sannan yace "D'ayar kuma yau ta shiga hannu na, d'ayan kuma kullum ina mata addu'a Allah ya kai rahama k'abarinta." Saida har ya fita lieutenant ya bi bayanshi yace "Kai ni fa uwar nan taka tsoro ma take bani, ua zanyi da ita ne?" "Kawo kunnenka kaji Abba." Mik'o masa yayi ya masa rad'a, saida ya gama ya kalleshi baki sake yace "Ammar kaji tsoron Allah, yanzu haka kake so na wa uwarka abinda ko da k'uruciya banyi ba." Da ido da gira ya masa alamar kawai yayi kafin yace "Abba saida safe, karna tsaya gyara tsofaffin hannu ni kuma na samu matsala." Da kallo ya bishi har ya fita, komawa yayi ciki ya sameta har ta kwanta, cire babbar rigarshi yayi ya shiga wanka, ya jima a ciki kafin ya fito ya saka doguwar riga ya zauna kusanta, hannu yasa ya tayar da ita zaune yana kallon fuskarta, cike da rarrashi yace "Sa'adatu na, fushin me kike yi dani haka har yanzu?" Kawar da kai tayi gefe ta k'ara tsuke baki, murmushi yayi yace "Haba uwar ya'yana, matar da babu mai irinta a duniyar nan, kiyi hak'uri mana ki daina hushin nan Allah ba kya kyau da hushi, kifa tuna bamu tab'a samun sab'ani ba da ke." Kallonshi tayi tace "Kasan da haka amma shine kan k'aramin abu zaka sauya min, naje neman sulhu kuma wai har kace min k'ofa a bud'e take na tafi baka rik'e ni, hummm." Matsawa tayi daga kusanshi shi kam dariya ma yake mata yanda d'an bakin nan ke masifa, sake rage murya yayi ya kama hannunta yana murzawa yace "Naji na d'auki laifina to a yafe min." Shiru tayi dan haka yace "Kinsan wani abu kuwa?" D'an kallonshi tayi lokaci d'aya ta d'auke idonta, cikin murmushi da son sauko da ita yace "Wallahi *uwar Amna* ina sonki sosai, ban tab'a sanin cewa ba kece ni ba sai da abun nan ya faru, dana zauna saina tambayi kaina, ashe dama ke ce kika sa na zama haka? Kin mayar dani babban mutum, kinsa na zama mai fad'a a ji a k'asar nan, kinsa na zama Baba har da kaka ma, ni kam a rayuwa me zan miki daya wuce na rumgumeki a k'irjina har mutuwa ta same mu a haka." Wuuuu (lieutenant kana wuta fa), Ummy fa tuni tajita ta saman bakwai akan gajimare tana shillawa, wallahi ya fasa mata kai sosai dan haka ta yafe ta hak'ura, kai idan ma da abinda yake buk'ata ya fad'a mata a shirye take, murmushin da bata shirya masa bane ya zo mata, yana ganin haka ya saki murmushin shima yana godewa wanda ya musu farrak'u tun farko.😂 *B'angaren amare* Da sallama ya bud'a k'ofar d'akin ya shiga, tsaya yayi yana kallonta da shu'umin murmushin da shi kad'ai yasan ma'anarsa, takowa ya farayi yana mata wak'a yana fad'in "*"Amarya ta ango wanene mijinta? Ammar ne mijinta, yau ga Hamna ga Ammar sai fa yanda ta yiwu." *Amarya ta ango wanene mijinta? Ammar ne mijinta, yau ga Hamna ga Ammar sai fa yanda ta yiwu."* Ita ba tayi dariya ba tayi kuka ba, takaici duk ya isheta ta kuma san gaskiyarsa fa sai yanda ta yiwun, ko motsawa ba tayi ba bare ta amsa mishi ko sallamar, aje ledojin hannunshi yayi ya shiga rage kayan jikinshi, kallonta yayi ko ina a rufe baya ganin komai, dan rigar ma ta bazu kan gadon kamar zata rufe shi dan dai yana da girma sosai, murmushi ya sake yi yace "Kankana ki rufawa kanki asiri ki cire mayafin nan kisha iska." Shiru kamar bata san yana yi ba, jinjina kai yayi yace "Komai bak'in cikinki dai Hamna yau kin zama tawa, nasan dai haushi kike ji na aureki ko? Ya kamata ki gane nine mijinki a duniya haka ma a lahira, kuma in baki manta ba dama na fad'a miki zanyi iko akan ki." Ko da ya gama ya shiga ban d'aki, wanka ya tsala ya d'auro alwala kafin ya fito, doguwar riga ya saka yana kallonta yace "Tashi kiyi alwala malamar k'arya, munafuka ta ganta a hannu duk ta nutsu sai salati take." Dan ta samu lafiyarsa cikin muryar data karyar da gabanshi tace "Bana sallah." Murmushi ya saki tare da mata kallon zaki gane kurenki ne yarinya, tappi ya shinfid'a ya kabarta sallahrshi, raka'a biyu yayi ya sallame ya sake kabbara wata yayi biyu ya sallame, saida ya kwarara addu'a ya kalleta ba tare data gyara ko da zamanta ba yace "Na aika miki taki kema." Tashi yayi ya fita sai gashi ya shigo da faranti, duk abinda ke cikin ledojin nan ya juye ya girke gabanta, bata ankara ba taji ya fincike mayafinta ya aje kan gadon yace "Gyara min zaman nan naki." A hankali ta d'aga kanta, wata irin fad'uwa gabanshi yayi sai yaga kamar ba ita ba, kyawun ya wuce misali har ido take d'auka, k'amshi kam kamar zai saka shi bacci, gyara zamanshi yayi ya b'allo k'afar kaza ya nufi bakinta da ita, girgiza kai tayi tana hararanshi, murmushi ya mata yace "Kiyi abinda kika ga dama zan rama, yanzu fara cika min cikinki." A hassala tace "Na ce bana ci Ammar." Wani kallo ya mata, a ranshi yace "Ammar, zaki daina zuwa anjima." Aje naman yayi yana kallon idonta yace "Kankana ko ki ci ki taimakawa kanki, ko kuma na d'ura miki da tsiya har sai kinyi aman wahala, ko kuma na baki ba sai kin b'ata hannunki ba, wane kika zab'a?" Idonta taji sun ciko da k'walla, hak'uri ta fara bawa kanta dan su rabu lafiya amma ba tace komai ba, sake d'aukar naman yayi ya kai bakinta, juya kai tayi tasa hannunta ta d'an tsakuro tasa bakinta, kallonta ya shiga yi yana ta cewa ta ci ta k'oshi, data tsaya saiya tsorata da cewa zai auka mata shi da kanshi, tun tana ci da yanga harta fara turawa da tsiya tana gangaro da hawayen bak'in ciki, saida taji ba zata iya ba ta kalle shi tace "Allah ya ishe ni haka." Sauka yayi daga kan gadon ya d'auki farantin ya fitar a waje, tana k'ok'arin saukowa daga kan gadon ya shigo, komawa tayi ta zauna tana gyara gyalenta, saida gabanta ya tsinke ya fad'i jin ya sawa k'ofar key, tsaf ya kashe wuta ya jaye doguwar rigarshi ya hauro kan gadon, da sauri ta fara kiciniyar sauka taji ya rik'e kafarta, cikin kunne ya rad'a mata "D'umi nake son ji kankana *uwar ruwa*." *Allah ya kawo ki ai.* *Idan naga comment zan... insha Allahu* 04/11/2020 à 14:39 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _71_ Cikin son k'watar k'afarta tace "Hannu zan wanke to." "Naga hannun." Ya fad'a yana kamo hannun, tana kallo ya saka yatsun biyun cikin bakinshi, lumshe ido tayi da sauri ta d'an d'aga labb'anta, a hankali kuma ta mayar dasu ta had'e wuri d'aya, tsikar jikinta taji duk ta tashi, wani yammmm taji tun daga tafin k'afarta har zuwa k'ok'on kanta, a hankali ta bud'a idonta har sun canza kala, kallonshi tayi sai kuma tayi saurin rufe idonta, cikin muryar da bata san tayi magana ba tace "Am..mar...sake ni." Cikin murmushin mugunta ya saki hannunta nata, a hankali yasa hannunshi na dama akan k'afarta yana shiga dashi cikin rigarta, da sauri taja k'afarta tace "Dan Allah Ammar." D'ago ido yayi ya kalleta, fito da hannun nashi yayi ya zauna da kyau tsakiyar gadon, fincikota yayi da k'arfi ta fad'o kanshi, suna had'a ido ta sako da k'wallan da suka mak'ale mata, cikin kuka tace "Ammar bana son haka fa." Gaba d'aya yasa hannayenshi ya tallabo fuskarta, bakinshi ya d'ora kan nata bakin ya shiga tsutsa a hankali, duk da ta ci abinci yanzu amma k'amshin chewing-gum spoot ya fi k'wacewa, a sannu sannu saiya fara mata horo akan labb'anta, Ammar? Sunan ne yake so yaji ta daina kira haka gatsau, da fari k'ok'arin k'watar kanta ta shiga yi, amma da taji slowly ne yake mata sai abun ya ratsa duk wata gab'a ta jikinta, shiru tayi tana karb'an tayinshi cikin girmamawa. Kamar abun arzik'i sai taji ya damk'o harshenta yana tsutsa kamar zai cira shi, numfashinta taji ya fara sauyawa kamar wacce asim zata taso mata, gashi dogon hancin shi ma ya rufe nata hancin, tana cikin son dawowa hayyacinta taji ya zage zip d'in rigarta, luma hannunshi yayi tsakiyar bayanta har yayi nasarar jan bras d'inta da k'arfi ya saketa ta b'alleta a baya, ba shiri ta bank'are ta gantsaro masa gaba hakan yasa shi bud'a ido ya kalleta, rufe idonshi ya sake yi yayi k'asa da hannayen rigarta da bras d'in, tsokar da Allah ya wadata bayanta da ita ya shiga matsawa yana cika tafukan hannayenshi da ita, har yanzu bai saki bakinta ba hasalima baida niyyar sakin, a haka kuma ya dawo da hannayenshi kan cikakken k'irjinta, taso sauke numfashin da bata san ko na menene bane, amma kuma babu dama saboda bakinshi na cikin nata, wani irin salo ne ya shiga mata yana shafasu yana d'an matsawa, cikin dubara ya kwantar da ita ya ci gaba da abinda yake, jin numfashinta na neman tsayawa yasa ta fara ture shi dan ta samu tasha iska. Da kanshi ya saki bakin nata yana kallon fuskarta ganin yanda take ajiyar zuciya, d'aya mamanta yasa a baki ya fara tsotsa kamar yaron goye, d'ayan kuma ya shiga lindashi hankali kwance, tureshi ta fara yi cikin d'aga murya take fad'in "Ammar ka rabu dani mana, wai miye haka dan Allah?" Wata k'ara ta kwamtsa iya k'arfinta sakamakon cizon daya sakar mata akan nono😂, zabura tayi zata tashi yasa tsintsiyar hannunshi ya danne wuyanta, a tsorace ta kalleshi cike da tausayin kanta tace "Dan Allah ka k'yale bana sallah fa." Wani kallo ya mata kamar maciji ya ga abun harinshi yace "Bari...na..duba da ka...ina." D'agata yayi ya fara shirin cire mata rigarta, tashi tayi zaune za tayi magana yaja duka k'afafunta da k'arfi hakan ya tilasta mata kwantawa kamar an tura ta, tsaf ya cire rigar tana ta k'ok'arin kare jikinta yaja zanin rufa ya musu shinge dashi, tana ji tana gani d'an pant d'in ma daya rage mata ya cire shi, kallonta yayi yana murmushi yace "Yaushe kika koma k'arya kuma?" Kawar da kanta tayi sai ji da tayi ya...😂 *kai ba da ni ba aradu.* Daren yayi ya tsala har ya raba amma har yanzu babu alamar zai sarara mata, to ita dai bata ga anfanin kuka da magiyar ba, tayi su har ta gaji ta barwa Allah, tana da tabbacin k'eta ce yake mata dan duk yanda akayi yayi anfani da wani abu, dan jarabar nan tafi k'arfin bil'adama, sai dai taji yana ta gumi zufa na tsatsafo masa ya kamkame ta, saita d'auka komai ya zo k'arshe, amma daya shiga ban d'aki ya fito saiya sake haye ruwan cikinta, tsabar fitina da jaraba har ban d'aki saida ya tallabeta ya kaita ya saka cikin baho ya tara mata ruwan d'umi, amma daya fito da ita ya sake juye, idonta sun kumbura tsabar kuka da kwana, ba idonta kad'ai ba duka fuskarta ta sauya kamanni, jikinta duk ya saki bata da wani katab'us sai yanda ya juyata, nonuwanta da gabanta tsabar zugi har ji take kamar suna barin jikinta ne. Sai dai a yau ta gane wane irin miji ta aura, lallai yer uwarta tayi hak'uri ba kad'an ba, yanzun haka kwance take ruf da ciki yana kanta ya samu hanya d'od'ar yana ta aiki, kwantawa yayi kan bayanta ya zuro da kanshi ya d'ora hab'arshi kan wuyanta yana kallon fuskarta idonta rufe cikin haki kamar wanda yake gudu, to wannan ma ai yafi gudu yak'i da arna ai ba k'aramin aiki bane da jihadi, cikin dariyar mugunta yace "To yaya...? Me ye ma suna na?" Ko da taji wannan tambaya ta gane inda matsalar take, ai da sauri dan ta ceci kanta tace "Yah Ammar." Cikin k'ara kaimin sukuwa yace "Um um, wani sunan nake so naji daga bakinki, suna na girmamawa da ladabi da kuma dad'i." Wani irin yunk'uri tayi kamar zatayi amai, da k'yar ta saisaita kanta ta luma kanta tsakiyar pillown da take kwance, ko k'arfin yin kukan ma bata da bare tayi, cikin muryar da bata fitowa tace " *Abban Shureim*, dan Allah yah Ammar ka k'yale ni haka, in ma baka so na ne wallahi yanzun nan zan bar maka gidan." Cikin kunne ya rad'a mata "Idan bana son ki kankana ina ni ina wannan k'ok'arin haka, yanzu fad'a min kina k'aunar d'ana ko har yanzu ba kya son shi?" Cikin matsanancin kuka tace "Ina son shi mana,d'ana ne fa." Saida ya cika hannunshi da tsokar bayanta yace "To ya kina so na?" Da k'arfi tace "Eh mana, ina sonka yah Ammar...wai Abban Shureim." Cak ya tsaya, a hankali ya zafe jikinshi daga nata yana dariya, saida ya sauka daga kan gadon ya d'aga hannunshi ya sauke mata mari a d'uwawu, saida ta zabura amma bata iya motsawa ba dan bata da wannan kuzarin, tana cikin addua'r ya shige ban d'aki ta samu damar labta mishi ashar taji yayi sama da ita ya shige ban d'akin da ita. Da ido kawai take kallonshi ya taimaka mata tayi wanka ya d'aureta cikin rigar wanka, fitowa sukayi yayi saurin d'auke zanin ya aje gefe ya d'auko wani ya shinfid'a ko kyau shinfid'ar ba tayi ba ya kwantar da ita, kallon fuskarta yayi ya sumbaci goshinta yace "Nagode sosai duniyata." Kiran sallah da taji yasa ta bud'a ido ta kalleshi, a hankali cikin dakusashiyar murya tace "Wace sallah ce ake kira?" Wani kallo ya mata yana murmushi yace "Kankana ya haka? Ko kan ya kwance?" Had'e fuska tayi ta kawar da kanta, mik'ewa yayi ya shiga ban d'aki yana fad'in "Asuba ce." Da kallon amma mutumin nan ya ci uban raina ni ta bishi, yanzu ita ya aikatar haka? Lallai bai nemeta da zaman lafiya ba, kuma zata nuna masa ita ma a shirye ta zo, lallab'awa tayi ta sauka daga kan gadon ta samu hijabi ta canza kaya ta kabbara sallah, dan dama cikakken wankanta tayi mai alwala, har ta idar da sallah bai fito ba, saida ta sallame tayi azkhar zata tashi ya fito, ko kallon Allah ya isa bata masa ba ta koma ta kwanta, tana jin kanta na mata ciwo haka ma zazzab'i na son rufe ta, amma haushi bai barta masa magana ba tayi ruf ta rufe. Tana ji yana ta kai da kawowa har bacci ya d'auketa dai, ko da ya gama shirin tafiya masallaci ya d'an jaye zanin rufar daga fuskarta, murmushi ya saki a ransa yana tausaya mata, ta fa jure sosai da bata mutu ba, amma hakan zaisa duk sanda zata masa magana sai tayi tunani ta taunata kafin ta fad'a, a hankali ya sunkuya ya sunbaci kumatunta ya k'ara gyara mata rufar sannan ya d'auki makullin mota ya fita. Daga masallaci ko da aka idar da sallah gari yayi haske ya fita. Bayan ya dawo kai tsaye b'angarensu Ummy ya nufa, ya samu bak'i da mutanen gida anata kayaniya, saida ya keb'e da uwa Zeituna ya bata wasu enveloppe guda hud'u, kallonshi tayi tace "Na miye yah Ammar?" Saida ya d'an lumshe ido yace "Uwa dan Allah ki daina kirana da yah nan." Murmushi tayi tace "Wallahi na saba ne, amma zan daina." Enveloppe d'in ya kalla yace "D'aya taki ce, d'aya a bawa mai kwalliyar data kwalle min amaryata, d'aya a bawa wanda suka raka min ita har d'aki na, kyauta ce daga gare ni." Cike da farin ciki tace "Kai masha Allah, mun ko gode sosai Allah saka da alkairi, har da ni a cikik kyautar?" Saida yasa hannu aljihu yace "Uwa ai kece gaba ma." Wani makulli ya mik'a mata tare da wata enveloppe d'in yace "Ki min k'ok'ari wannan ki bawa yarinyar nan, ni dai ba zan shiga gidan can yanzu ba mu had'u da ita." Dariya tayi ba tace komai ba, dan ita ma ta gama fahimtarshi kamar yanda uwarshi mahaifiya ta gama sanin shi, ko da ya fita ta samu Ummy ta nuna mata, taji dad'i sosai na wannan abu da yayi, amma ita ma sai tace ta nunawa Hajia sannan a bawa masu hakk'in, Hajia ma ko da ta gani cewa tayi "Mai abun arzik'i kenan dana tsiya, Ammar ikon Allah." Sanda aka gabatar da kyautar ga masu ita gidan ya sake kaurewa da shewa, mai kwalliya tafi kowa murna kam dan kyauta da aka bata ba k'aramar tsoka ne da ita ba, Zeituna da kanta taje dan damk'a amanar da aka bata, bacci ta samu tana yi wanda kallo d'aya ta mata ta bala'in jin tausayinta, dan iya fuskarta kawai da duk ta kumbura zaka gane ta wahaltu, ba dan sallamar da tayi ta tashe ta ba da juyawa ta so tayi, amma tunda ta farka kuma tace ta shiga haka ta samu wuri ta zauna kusa da ita. D'an k'ara kallonta tayi tana kwance tace "Sannu Hamna, ba kya jin dad'i ne?" Saida tayi kamar zata tashi kuma ta koma tayi lamo kan gadon, cikin galabaita tace "Ba komai aunty Zeituna, antashi lafiya?" "Lafiya lau, ya kwanan bak'unta?" K'ala ba tace ba sakamakon wani zuuuu da taji k'asanta ya mata, iska ta dinga furzarwa mai zafi tana d'an matse fuskarta, Zeituna dai na kallonta ta fito da enveloppe d'in da makullin ta mik'a mata tana fad'in "Gashi." Kamar wacce ke ciwon nak'uda tace "Aje min nan, na miye?" A hankali tace "Inji yah Ammar." Jim tayi ko kallonta ba tayi ba, tashi tayi da niyyar fita sai ganin Hamna tayi ta tashi da k'arfin tsiya da gudu ta shiga ban d'aki tana kakarin amai, da sauri ta bita ban d'akin tana kallonta yanda take kwaranya aman wahala, ko da ta idar ta durk'ushe ciki da sauri ta kamota suka fito, tana zaunar da ita bakin gadon tayi kwance dan bai zaunuwa gare ta, cike da kulawa Zeituna tace "Sannu Hamna, bari na wa aunty magana sai ta zo ta duba ki." Tana kwance ta rufe fuska da zanin rufar kunya ma duk ta isheta, a zuciyarta tana fad'in "Ammar d'an bala'i ne,amma zata rama wannan wulak'ancin." Bata ankara ba kawai taji amai ya sake gabce mata akan gadon bai ko bata damar tashi ba, ta yunk'ura zata tashi tsaye Ummy ta shigo tare da Zeituna hankali a tashe, da sauri ta k'arasa gareta tana fad'in "Subhanallahi Hamna, ba kya jin dad'i ne?" Har zata zauna bakin gadon Zeituna tace "Bari na d'auke zanin a canza wani saiki dubata." Tallabarta Ummy tayi suka tsaya ta d'auke ta shinfid'a wani, kwantar da ita sukayi Ummy data shigo da d'an akwatin magani na tafi da gidanka ta shiga duba ta, mugun zazzab'i ta samu a jikinta, ga ciwon da tace kanta na yi ga amai, uwa uba kuma da tace bata iya zama, ba b'ata lokaci ta d'aga doguwar rigar data saka ta abaya ta dubata, saida ta dafe goshi cike da jimami ta kalleta da matuk'ar tausayawa tace "Hamna hak'uri zakiyi, wallahi sai an miki k'ari." Da sauri ta shiga girgiza kai tana fad'in "Ummy bana so, Allah ni dai bana so ki barni hakanan." Cikin lallami tace "Kiyi hak'uri mana Hamna, idan ba'a miki ba kema ai ba zaki ji dad'in jikinki ba, ki daure kinji." Ita ma dafe goshinta tayi ta cije leb'en k'asa ba tace komai ba sai wani numfashi da take saukewa, Zeituna ce tace "Kin ci wani abu ne?" Ido rufe ta girgiza kai, da sauri ta mik'e tace "Bari na samo mata wani abu kafin tasha magani." Cikin jin dad'i Ummy tace "Yawwa Zeituna kin kyauta." Tana fita Ummy ta kalleta tace "Hamna halan halin naku kuka siyar?" Girgiza mata kai kawai tayi dan haka tace "Gardama kika masa?" Nan ma kai ta girgiza alamar a'a, cikin jin haushi tace "To me kika masa ya miki wannan zuwan haka?" Cikin zubo da hawaye ido rufe tsabar kunya tace "Ummy ban masa komai ba, kawai dai abinda na lura ya hora ni ne saboda sunansa da nake kira." Hannunta ta rik'e tana fad'in "Yi shiru to ya isa, kiyi hak'uri kinji, zai dawo gidan ya same ni ai." Magunguna ta fito wanda zata bata da allurar da zata mata da kuma ta d'inki, ko da Zeituna ta kawo mata soyayya k'wai had'e da dankalin turawa da tea had'in kauri ya ji madara, saida tsiya Ummy ta matsa mata ta ci sosai kafin aka shiga aiki, Zeituna uwar tausayi sai gashi ita ma kuka ita Hamna kuka, ba tace taji haushinshi ba kam, amma dai ta tausaya ma yarinyar irin wannan tashin hankali haka, ko ita data auri ubansa ai ko rabin wannan jigata ba tayi ba, maganin bacci Ummy ta bata tasha ba jimawa ya d'auketa cikin salama. Ajiyar zuciya ta sauke mai k'arfi tare da girgiza kai, kallon Zeituna tayi dake share hawaye ta kece da dariya tace "Kinga aikin yaron naki ko? A hakane kuma baki son ganin laifinsa." Hanyar fita tayi tana fad'in "Muje to ki wanke fuska, tunda yau dai d'an naki yasaka ki zubar da hawaye." Cikin basarwa Zeituna tace "To aunty mutum da matarsa, sannan kinsan halin 'yarki taurin kai ne da ita." "Duk taurin kanta sai kiyi duba da d'an mutum fa ya tsaga ya fito ta gabanta, amma a hakan ya mata wannan cin wulak'anci, me kike tsammani idan da budurwa ce? Da kenan gawarta ce muka wanke yanzu?" Dariya dai Zeituna tayi dan gaskiya ta fita gaskiya yau kam. Safiyar ta yau Jibril dake d'an alak'a dasu ne ya samu labarin rasuwar malam Rabi'u, Labaran ya fara fad'a ma maganar, cewa yayi zai je amma idan Hajiarshi ta amince, yasan kuma ba lallai ta amince ba shiyasa yaje da kanshi, ya jima yana bata hak'uri da bata baki kafin ta yarda su tafi, Labaran da Jibril da Jamil tare da Soueiba da Hajia suka tafi, Husseina ta so Hajia tayi zamanta amma tace to in mutuwa bata zamar mana wa'azi ba me kenan zai ladabtar damu? Haka suka je wajen gaisuwa daga nan kuma har suka je gidansu Mari ganin mamarta. Jikinta yayi kyau yanzu fiye da da kam dan maganarta ma lafiya lau sai abunda ba'a rasa ba, sai Mari da suka samu tana kan sharholiyarta, ta k'ara mulmujewa tayi jiki sosai, da gani kuma kasan k'ugunta yanzun na magani ne, ta shiga shafe shafe tayi jawur kamar zabiya sai dabbara dabbara na musamman a hannayenta, ta k'ara huje a kunnenta barkatai abun har ya k'azamce. Sanda suka je bata nan suna zaune ana ta gaisawa da hirar ya bayan rabuwa sai gata ta shigo tana waya, atamfa ce jikinta amma har gwara wasu kayan na kanti akan na jikinta, siket d'in yanda ya kamata kai kace bata iya tafiya, ya fito mata da bankamemen k'ugun nan kam har saiya baka tsoro, rigar kuwa duk rabin nonuwanta a waje suke sun matsu sunyi pam dasu, baya ma haka duk rabinshi waje yake dan haka ko bras ma bata saka ba, atach ne akanta babu kitso ta d'aure da ribom, kwalliya ce ta tashin hankali a fuskarta da gani kasan ko dai biki zata je ko kuma ta dawo ne, duk da ta ganesu sarai amma cike da wulak'anci ta wuce d'aki tana fad'in "Sannunku." Girgiza kai Jibril yayi ya d'an kalli Mamanta, daga kallon da yaga tabi ta dashi zai fassara maka abinda take ji game da hallayarta, sai yaji tausayinta ya kama shi sosai, da zata amince shi kam daya d'auketa sun tare a sabon gidanshi da zai koma, ko ba komai dai akwai alak'a tsakaninshi da ita. Ko da suka gama gaisuwa suka tashi dan komawa, sallama sukayi sosai suka fita, a soron gidan suka ji ance "Jibril." Kusan a tare suka juya dukansu, Mari suka gani da d'aurin k'irji na towel kalar pink, dukansu fita sukayi suka barsu, d'auke kanshi yayi daga gare ta, cikin wata shegiyar murya tace "Huda nace ko zaka kawo min ita idan an musu hutu ta zauna tare dani?" Ba tare daya kalleta ba yace "Ba zai yiwu ba gaskiya, amma dai in aka sake sun zan turota tare da dreba ya kawota, zai kwana anan shima kwana biyu sai su koma tare." Da mamaki ta kalleshi tace "Ban gane ba? Kana nufin ko wata ba zaka bari ta min ba?" Bai kalleta ba yace "Ba zai yiwu ba nace, sai anjima." Ya juya zai fita tace "In ka isa Allah ya tsine min, to me kake nufi dani? In haifi yarinyar a ciki na kace zaka min iko akan ta, Allah baka isa Jibril ko da k'arfi zan k'waci 'yata." Juyowa yayi ya kalleta sama da k'asa yace "Ni ba sakarai bane Mari, da kin nutsu kin gyara halinki da Huda ta zauna tare da ke, amma a halin yanzu na kawo miki yarinyata mace mai shekara goma sha biyu a duniya, c'est très difficile Mari." Juyawa yayi ya fita me Mari zatayi sai kuwa ta fara nuna halin rashin kunya da fitsara, har k'ofar gidan ta fita da d'aurin k'irji ta shiga aika mishi munanan ashar, shege tsinanne bak'ar haihuwa ai duk shi ya lalata idan ya manta ta tuna masa, shine yanzu zai mata iko da d'iyarta to bai isa ba, su dai babu wanda ya kulata tuni sukayi nisa ma sai ita suka bari tana haukanta, sai dai yayi niyya ba zai ma kawo Huda ko da tayi kwana biyun bane, zai kira mahaifiyarta ya bata hak'uri tunda ita ma tana son ganin Huda, amma yasan inya kawota tana iya rik'eta hakan kuma zai haifar da tashin hankali, dan akan tarbiyar yarsa zai uya makata kotu ma ta rabata da ita har abada, dan yana mugun son yarinyar yana kuma bata kulawa, duk wani motsi nata a lure yake dashi da taimakon Jamila da yanzu take d'aukar yar kamar nata yaran, sai dai kawai k'addara da kuma yaran zamani da wani lokacin sai su fi iyayen da suka haifesu dubara ma, amma har yanzu yana addu'a Allah ya yafe masa abinda ya aikata a baya ya kuma shirya masa yaransa da sauran zuri'a. Har azahar bai dawo gidan nan ba saida Ummy ta kirasa ta masa wankin babban bargo, dariya kawai yake mata yana cewa tayi hak'uri to taja wa yarta kunne ta dinga girmama shi, a k'arshe dai tace an k'i aja d'in ya jima bai kasheta ba, sai kusan k'arfe biyu da rabi ya shigo gidan da matuk'ar bacci a idonshi, kai tsaye d'akinta ya shiga ya sameta kan sallaya kwance dan zaman salla ma da k'yar take d'an azawa saboda d'inki hud'u Ummy ta mata, zaune yayi k'asa kusanta ya dafata yana fad'in "Ayyah beby sannu, ashe baki da lafiya? Kai amma wallahi banji dad'i." Ko kallonshi ba tayi ba bare ta amsa mishi, tallabota yayi ya tayar da ita zauna, da sauri ta rintse ido tace "Washh." Cikin dubara ta d'an zauna rabi da rabi yanda bata jin zafin sosai, shafa kumatunta yayi yace "Sannu kinji, me ya same ki ne haka? Waya tab'a min ke?" Idonta cike da k'walla ta kalleshi, da Allah zai ara mata lokaci da cakumar wuyanshi zaatayi sai taji ya daina motsi, sai dai bata da wannan k'arfin a yanzu kam watak'ila ko a gaba, janye hannunshi tayi daga kan kumatunta ta tashi da k'yar ta nufi gado, wannan enveloppe da makullin ta d'auko ta cilla masa a jiki tace "Ka rik'e bana so." Mik'ewa yayi tsaye yana d'aukar kayan yace "Ban gane na rik'e ba? Naki ne fa." A k'ufule ta kalleshi tace "Shine nace bana so, ai kasan nafi k'arfinsu ko tunda ni ba ci ma zaune bace, sannan ubana ya d'auke min nauyin komai." Tab'e baki yayi ya aje mata kan gadon yace "Ni ma kuma idan nayi abu na bashi baya kenan har abada, ko ki rik'e ko ki jefa a kwandon shara ruwanki ne, ni ladar wahalarki ce na biyaki." Da wani mahaukacin mamaki ta bud'e baki tana kallonshi, ladar wahalarta? Me ya d'auketa to? Tana cikin tunanin taga ya fice a d'akin yana hamma, a hankali ta fita daga d'akin ta bishi d'akinshi daya shiga, ko da ya juyo ya kalleta yayi murmushi yace "Har kin fara nema na da kanki madame?" Sama da k'asa ta harareshi tana kallo ta ga me zaiyi, tsaf ya haye gado har da jan zani ya rufe, murmushi ta saki mai ciwo kafin ya kalleta yace "Idan aka kira sallah la'asar ki tashe ni." Da kallo kawai ta bishi tana tsaye bata gusa ba, tun yana kallonta yana murmushi har ta ga idonshi rufe dai alamar yayi bacci, cikin takonta na hankali kwance ta shiga ban d'akin ta d'ebo a murfin butar dake ciki ta fito, saida ta tsaya kanshi ta juye masa ruwan a fuska. *Aiki ya kwaso ki Hamna.* Da k'arfi ya firgita ya tashi yana zazzare ido yana kallonta, cikin goge ruwan fuskar tashi yace "Ke lafiyarki k'alau? Me ke damunki?" Saida ta rik'e k'ugu tace "Abinda ke damunka." "To miye haka?" Ya fad'a da k'arfi, tab'e baki tayi tace "Babu ta yanda za ayi kayi bacci wallahi bayan ni baka barni bacci ba, haka kawai." A nutse ya kalleta yace "Hamna zaman lafiya kike so ko tashin hankali? Duk wanda kika zab'a shi zan zage damtse na nuna miki, tunda ni har siyarwa nake kuma ina koyar dasu." Wata yar dariya tayi tace "... *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:39 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _72_ "Duk wanda kake ji nima shi nake ji." Murmushi yayi yana sauka daga kan gadon yace "Hum!" Fita yayi daga d'akin ya koma falo, nan ma ko da ya kwanta kan kujera tayi tsaye ai babu shi babu bacci, tashi yayi ya koma d'akin yasa key da sauri, babbugawa ta shiga yi tana kiran ya bud'e, dariya ya mata yace "Indai kina da zuciya ki rabu dani, na gane me kike buk'ata yarinya, tanadi nake miki har a jima da dare saina b'arar miki da ita." Hak'ura tayi ta kwanta a falon ita ma, ko da aka kawo mata abinci ta ci ta sake shan magani dan jaraba ce kawai amma tana jin jikin sosai. Bata jimawa da kwantawa ba kawai amai ya sake taho mata, da gudu ta shiga ban d'akin dake falon d'an nesa da madafa, jin kakarin abun yake daga sama ba sosai ba, tasowa yayi yana fitowa ya tabbatar da abinda yake zargi, tsaye yayi yana mata dariya har ta ida ta juyo zata fito, wurga masa harara tayi zata fita yace "Madame ki fad'i gaskiya mana, duk yanda akayi an sake samun k'aruwa ne." Wani kallo ta masa tace "K'aruwa fa, da kai? Shikenan dan na zama kaza daga tab'a ni sai d'aukar ciki? Allah ya sawak'e." Hannunta ya kama tana ta k'ok'arin k'wacewa amma ya rik'e gam, saida ya kaita har d'akinshi ya kwantar da ita kan gado, k'afarta taga ya d'aga yana shirin saka mata hannu, da sauri ta yunk'ura ta tashi tana fad'in "Malam lafiya?" Kallonta yayi fuska a had'e yace "Kwanta." Cike da tsiwa tace "Na k'i na kwanta d'in, Ammar ka rabu dani mana." Sam babu alamar wasa ko walwala a fuskarshi ya sake kallonta, hannu yasa ya kwantar da ita da k'arfi ya taushe da hannu, hannu ya zura cikin rigarta ya janyo pant d'inta ya jefar, ihu ta fara tana fad'in "Allah ka k'yale ni banda lafiya, Ammar kashe ni fa zakayi, wai kai baka da iman...?" Da sauri taja bakinta tayi gum tare da rintse ido sosai, ta d'auka ita ya kaiwa wannan naushin, ashe gado ya daga dan shi kanshi ya so d'auketa da mari, amma ya kasa baisan me yasa ba? Idonshi jawur ya kalleta ya juyo da fuskarta zuwa kallonshi da k'arfi yace "Kalle ni nan." A hankali ta bud'a idonta ta sauke akan shi, rarraba ido ta shiga yi tsoron yanayinshi ya shiga zuciyarta sosai, a hassale sosai yace "Akan me zan bani umarni gaba da gaba ki fad'a min ba zakiyi ba? Wacece ke Hamna? Me kike ji dashi da zaki dinga min abinda kika ga dama?" Rikicewa tayi ta rasa tunaninta baki d'aya, cikin had'iyar yawu masu d'aci tace "Bo...sss, kayi hak'uri dan..." Cikin daka tsawa yace "Waye Boss d'in?" Da k'yar ta d'aga labb'anta tace "Abb..." Sai kuma tayi shiru ta kasa k'arasawa ta fashe da kuka, kallon fuskarta yayi sosai yanda take kukan da gaskiyarta, a take yaji gwiwarshi tayi sanyi zuciyarshi ta raunata sosai, sai kuma yaji haushin kanshi na kukan da take yi dalilinshi, a hankali ya d'an d'agata ya koma gefenta ya kwanta yasa hannu yana share mata hawaye, ture shi ta fara yi amma me Ammar zaiyi saiya shiga manne mata yana rik'eta a jikinshi gam. Ita ba tayi shiru ba kuma bata tsaya ba, kallonta yayi a raunane ya sassauta muryarshi yace "Kiyi hak'uri kinji, ba zan sake ba to na miki alk'awari." Da wani fitinanne mamaki ta kalleshi, Ammar ne ke bata hak'uri har da alk'awari? Lallai duniya juyin waina ce, ganin yanda take kallonshi yasa ya k'ara rusunawa yace "Eh kiyi hak'uri, ba zan sake saka ki kuka ba, *Hamna ki fahimci rauni na akan ki mana*, wallahi kina da mahimmanci a zuciya ta, amma ba zaki gane ba yanzu saboda nasan kin tsane ni." Sake mannata yayi a k'irjinshi yana ci gaba da shafa kanta, jin tayi shiru sai ajiyar zuciya take saukewa, wallahi ji take kamar ta k'urma ihu dan dad'i, *Ammar ne ke mata kalamai haka da sanyi sosai, kuma sanyin ma ba mai cutarwa ba? Lallai ta yarda ita d'in wata ce a zuciyarshi, to ko wannan dalilin ne yasa bai cika saurin kaiwa jikinta ba kamar yanda yake da saurin kaiwa a jikin yer uwarta? Amna har dukanta ya tab'a yi amma ita iyakarta dashi mari a fuska, wuuu!*. Bacci na neman d'auketa kan k'irjinshi taji yace "Ya kike jin jikinki yanzu? Da sauki ko na kaiki asibiti?" Saida ta turo baki gaba ta rufe idonta kamar tayi bacci, jin bata bashi amsa ba yasa shi lek'a fuskarta, k'ura mata ido yayi ganin tayi wani fauuu da ita, a hankali ya d'ora bakinshi kan nata ya sumbata, sake kallonta yayi yace "Bakin kamar chocolat, *ina sonki* amma baki da hankalin da zan fara bani kisan al'amarin nan a yanzu." Sake tura kanta yayi ya ci gaba da shafata, sai tayi kamar ta farka kuma ta daure tayi shiru, Ammar? Yana so na? K'wafa tayi a ranta tace "Lallai ma mutumin nan, ba zai fad'a min ba saboda banda hankali, ai kuwa ka shiga ukunka wallahi." Haka ta wuni a galabaice babu lafiya, da dare ko da ya shigo a gajiye shima yayi zaune kan kujera yana kallonta, rigar kanti ce ta saka marar nauyi wacce ta dace da ita, ita dai bata ce dashi komai dan haka yace "Kankana me kika dafa ki kawo min na ci? Yunwa nake ji sosai." A wani yamutse ta kalleshi tace "Me na dafa? Ai kai zan ma wannan tambayar me ka shigo min dashi? Ina fama da kaina ne zan tafi maka d'ori?" Kallonta yayi na yan dak'ik'u, lallai da aka ce kar Allah ya kawo ranar yabo, a take ya tuna da Amna sanda take amarya, da kanshi yace kar tayi girki amma saida tayi, murmushi yayi a ranshi ya mata addu'a kafin yace "To me kile so na siyo miki?" Saida ta kalli tsakiyar idonshi tace "Kaza." Wani kallo ya mata yace "Kaza kuma? Bayan wacce kika ci jiya?" Saida ta d'an d'ago daga kan kujerar tace "Eh na ci cin dole ba, kuma aikin da kayi ai yafi na kazar da na ci, dan haka siyo min yanzu na ci na darje." D'an cije leb'en k'asa yayi yana mata kallon zaki ci kaza kam, mik'ewa yayi ya fice ta bishi da kallo, dariya tayi tana jinjina kai da cije leb'e. Yana kan hanya ta kira wayarsa, yana d'auka tace "Boss na manta nace ka had'o min da ice cream na vanilla da yaghurt." A kasalance yace "To, ki fad'i duk abinda kike so ma." "Shikenan." "Ba damuwa." Ya fad'a yana kashe wayar. Ko da ya dawo ya girke mata komai gabanta ya aje, saida ta sauko k'asa ta gyara zamanta dan yunwa take ji ta shiga bawa cikinta hakk'inshi, yana kan kujera yana kallon yanda take d'urawa yana girgiza k'afafu, ita ma lokaci lokaci ta kan kalleshi saita harare shi ta ci gaba, murmushi ya mata yace "Ashe haka kike dan tsiya shiyasa kike zama rusheshiya". Da sauri tace "Tubarkallah." Murmushi ya sake yi yace "Yi sauri ki gama ci to ni sai na ci acan." Sama da k'asa ta harare shi tace "K'arancin aikinyi ne matsalar ko? Allah ya kyauta." Wani basaraken murmushi ya shinfid'a kan fuskarshi, kallo yake mata na zaki gane baki da wayo, ya zama dole ki dinga gyara harshenki kafin ki min magana, saida ta gama bata damu shi ya ci d'in ba da yace yana jin yunwa? Idan ya ci a ina ya ci ko me ya ci? In kuma bai ci ba me zai ci to tunda kazar guda d'aya ce? Ko a jikinta tana kammalawa ta mik'e ta shiga madafa ta wanke hannunta ta dawo, d'aukar ice cream d'in tayi ta shige d'aki inda ya bita da kallo yana fad'in "Iyee! Hajiar nan fa kin tara manyan kaya." Ko juyowa ba tayi ba sai ma gyara tafiyarta yanda ta sake d'aukar hankalinshi, tashi yayi ya shiga d'aki yayi wanka ya shirya, dogon wando kad'ai ya saka ya fito ya shiga d'akin, tana kwance tana shan ice cream d'inta hankali kwance, fizge robar yayi yace "Ruduwar wofi, kina mace zaki saka abun sanyi gaba kina ta sha babu ragewa, dan mugunta ni kike so na kwashe miki matsalar ko?" Zaune ta tashi tace "Amm..boss bani kayana." Aje robar yayi gefenta ya zauna kan gadon yana shirin kwanciya, zunbur tayi zata sauka ya rik'ota, zillewa ta shiga yi da iya k'arfinta amma saiya k'ara matseta yace "Ke." Kallonshi tayi tana turo baki, d'orawa yayi da "Ki bini sannu ko na karyaki." A hankali tace "To sake ni na fita." Wani kallo ya mata yace "Akan me? Kin manta kin ci kazata ne?" Girarta ta had'e wuri d'aya kamar ta tambaye shi kuma tayi shiru tana d'an mutsu mutsu, zanin rufar ya janyo ya rufe su cikinshi, take idonta ya raina fata ta fara sako hawaye, cike da muryar rarrashi tace "Dan Allah yah Ammar yi hak'uri ka k'yale ni, banda lafiya fa ka sani." Murmushi ya mata ya kwanta ya d'ora kanta kan k'irjinshi yana fad'in "Wacce bata da lafiya ce ta iya cinye kaza d'aya? Abun da mamaki." Hannunshi yasa cikin rigarta ya kamo albarkatunta ya fara shafasu a hankali yana lumshe ido, d'ago kai tayi ta kalleshi tace "Dan Allah kayi hak'uri, ko ina ciwo yake min." Kallonta yayi yace "Da gaske? Na gani to." Hannuwan rigar yayi k'asa dasu ya bud'e rufar dan ya gani da kyau, a hankali ya shiga kallon k'irjinta kuma in har zai fad'i gaskiya sunyi jawur tsabar wahala, ba iya jan ba kawai sai ya ga kamar sun kumbura ga sawun cizon daya mataa d'ayan, har saida bugun zuciyashi ya sauya tsabar tausayinta, amma a zahiri dariya ya mata ya sake kaisu bakinshi yana tsutsa, ita kuma duk tsutsar da yake ta lik'e ido jim saboda kamar ciwo ne ake fama maka shi. Ba tace mishi komai dan tasan dagangan ne yake yi kawai, amma da taji yana neman rabata da pant d'inta da sauri ta bud'a ido ta rik'e hannunshi da duka hannayenta tace "Dan girman Allah *ubana yarana* ka rufa min asiri, wallahi fama ni zakayi." Cire hannayenta yayi daga nashi ya shiga zare mata pant d'in, kuka ta fara dan ita dai ba k'arfi ne da ita ba bare ta kare kanta, kukan kawai ta fara yi tsakaninta da Allah, saida ya zage mata ya kalli fuskarta da kyau, kukan na tab'a shi sosai har idonshi sun fara taruwar ruwa ruwa alamar shi ma kamar zaiyi kukan, sai kuma ya d'an matse ido yace "Hamna ba kya jin magana ta, kin raina ni baki san me zaki fad'a min ba, bana son haka ina yawan fad'a miki, amma bansan me yasa kike da taurin kai ba, ba zan iya dukanki ba saboda ni ne zan wahala, amma kin kasa fahimtar haka, bansan ya kike so nayi da rayuwata ba?" Cikkn kukan bala'i murya a tausashe tace "Kayi hak'uri yanzu zan dinga ji, wallahi zan ji maganar ka na maka alk'awari." Girgiza kai yayi yace "Ba fa jiya ko yau bane na fara saninki, ina rabuwa dake zaki gudu ki ce min Allah ya isa kinje kinyi." "Wallahi ba zanyi ba, na rantse maka da Allah ba zan kuma yi maka rashin kunya ba." A hankali ya kai yatsarshi da tafi tsayi luma cikin gabanta, wata irin zabura tayi tace "Aahhhhhhhhhhh..." Yanda ihun ya daki dodon kunnenta yasa shi saurin rufe mata baki, zazzaro ido tayi tana kallonshi sai ya ga hawayenta na yanzu ko k'akk'autawa basa yi suke zuba, cikin kunne ya rad'a mata "Shiiii! Me ye haka?" Ba tare daya d'auke hannunshi daga bakinta ba cikin rad'ad'in bala'i tace "Ka da ka fama ni *yallab'ai*, za...fi." Shi kam baisan me ke nan ba saiya shiga yawo da yatsarshi sai yayi kamar zai fito dashi ya koma ya mayar, lokacin da shi kanshi ya d'an fara jin alamun kamar zare na d'an tab'a mishi hannu yana jin wurin da tauri tauri yana d'an sukarshi yasa shi kallon fuskarta, duk da kwance take amma duk ta k'ame wuri d'aya sai jan numfashi take tana ta girgiza kai, a nutse yace "D'inki Ummy tayi miki?" Da sauri ta shiga d'aga masa kai alamar eh, a hankali ya jawo yatsarshi ya cire, kwance yayi kusanta ya rumgumeta kamar zai fashe da kuka yace "Kiyi hak'uri kinji, ban sani ba ai, Ummy bata fad'a min ba ke ma haka." Hamna da a lokacin take wa kanta hud'ubar zaunawa dashi lafiya saita k'ara ruk'umk'ume shi da hannunta da ba kanshi take kwance, tusa kanta ta shiga yi cikin k'irjinshi tana ta damuk'ar damtsenshi tana kuka, rirrik'eta yake yi sosai yana bata hak'uri, a haka bacci ya d'auketa tana ajiyar zuciya. Ko da ya tashe ta da asuba ta bud'a ido ta kalle shi, doguwar riga ce jikinshi da sallaya hannunshi, yar ajiyar zuciyar data sauke ta tuna mata da kukan data kwana tana yi da kuma dalilin kukan, ai da sauri ta tashi zaune tace " *Ina kwana*...boss." Wani kallo ya mata mai d'auke da yanayin mamaki a cikinshi, ba tare daya nema ba Hamna ke gaishe shi, amma sai ya d'an basar yace "Me ye kuma boss? Hamna ba zaki daina min wannan sunan ba?" Langab'e kai tayi tace "Kayi hak'uri ka bani dama na ci gaba da kiranka haka, kai ma ai har yanzu kana ce min kankana." Murmushi kawai ya saki ya nufi hanyar fita yana fad'in "Ki tashi kiyi sallah." Da kallo ta bishi har ya fita, data shiga ban d'aki saida ta had'a ruwan d'umi ta jima zaune a ciki, wanka tayi tayo alwala ta fito ta kabbara sallah. Har rana ta take ta hantse bai shigo, ta tashi da niyyar shica madafa ya shigo da kular abinci a hannu, mik'a mata yayi yace "Inji uwarki." Kallonshi tayi a ranta tace "Kaji wai inji uwarki? Ina ma laifin ka ce Ummy ko mamanki, hmmm Allah ya sawake." Ajewa tayi kan tebur ta juya zata shiga d'aki yace "Ina zaki je?" Juyowa tayi tace "Wankan zanyi." Saida yaje gabanta ya kama hannunta suka shiga d'akin tare, ita dai gabanta na fad'uwa haka ta daure ta bishi, har ban d'aki suka shiga cikin kwanciyar hankali ya rabata da komai shi ma haka ya fara wanke tsaf. Wani hegen siket ne da rigarshi na kanti ya matseta ya saka mata, saida suka fito falo ya zauna kan kujera yana kallon tv yace ta kawo abincin nan, juyawa tayi ta fara bada step (inji malam ba), a hankali ya shiga lumshe idonshi yana bud'ewa yana sauke su kan k'ugunta, kutumar bala'i sai yau ya k'ara tabbatarwa ba k'arama bace, haka ta d'auko ta dawo ya shiga kallon gaban da komai da komai. Har k'arfe *09:00* yana gida ta zubawa sarautar Allah ido, ta gaji ta k'agu ta k'ufula ta jigata da matsar da yake mata, duk jikinta ji take kamar wacce tayi nak'uda, labb'anta banda zafi da zut zut babu abinda suke, sai yanzu kad'ai ya shirya fita ya kama hannunta har k'ofar d'akin, bud'e hannayenshi yayi yace "To rumgume ni ki min addu'a zan fita." Wani kallo ta masa da shi dai ya fassara shi kallon baka da hankali ne, a hankali ta bud'e hannayenta ta fad'a k'irjinshi kamar mai k'yank'yaminshi😂 kafin tace "... *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:39 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _73_ "A dawo lafiya." Tallabo fuskarta yayi yana murmushi yace " *Je t'aime* (ina sonki)." K'wayar idonshi ta kalla, ganin shima ya kalli idonta sai tayi k'asa da nata tana murmushin da bata san damilinshi ba, sake d'ago kanta yayi yace "Ke ma ki ce wani abu mana." Da sauri ta kubce daga rik'on daya mata ta juya zata shige ciki, hannunta ya rik'o ya sake had'ata da jikinshi yace "Idan baki ce komai ba zan dawo ne mu zauna tare, kuma ke dai kinsan me zai faru." Juyowa tayi tace "Kunya nake ji mana." Sakin hannunta yayi yana murmushi yace "Su kunya manya, ita ma yau ranarta ta zo." Juyawa yayi ya fita yana fad'in "To Allah ya bamu irin ta ku." Juyawa tayi ta bishi da kallo har ya fita, dawowa tayi ta ma kanta mazauni kan kujera, a hankali take sauke numfashi had'e da murmushi a fuskarta, ta ji dad'in kalmar sosai data fito daga bakinshi, wani nauyi taji ya ragu a kanta data jima tana dakonshi a zuciyarta. Tana cikin tunanin nan ta shiga d'aki ta shirya ta fito dan shiga wajensu Ummy ta ga lafiyar yaranta, tasan Ummy ce ta rik'esu dan a bata damar morar ranarta ita ma, shiyasa ko mitsinsu bata ji ba daga randa aka kawota zuwa yau. Da sallama ta shiga falon ta samu Ummy tare da Hajia zaune da Husseina, k'arasawa tayi ta gaishe su suka amsa da tambayarta ya take ita ma? Ummy ta kalla tace "Ummy ina yarana suke?" Kallonta tayi tace "Kin manta suna islamiyya?" D'an turo baki tayi tace "Ummy me yasa basu tafi gani na ba?" Ba tare data kalleta ba tace "Zasu tafi, amma ba yanau ba." Shirun da tayi yasa Ummy kallonta tace "Ya jikin naki?" Saida ta sunkuyar da kanta tace "Da sauk'i Ummy." Jinjina kai tayi kafin su ci gaba da hira, ita ma nan tayi zamanta har Zeinab da su Jamila suka shigo sukayi ta hirarsu. *Bayan sati uku* Ya shigo kenan ya had'u da Zeituna zata fita, sauke gilashi yayi yace "Uwa ina zuwa da rana haka?" Saida ta gyara goyon *Shakur* tace "Wallahi kasan Jumare ta haihu, zan tafi can ne yau ake sunan." Da dariya a fuskarshi yace "Iyee! Su Jumare manya, to uwa ina motar naga zaki fita k'asa?" Cikin damuwa tace "Saida na gama shiri zan fita kuma sai Ayuba yake fad'a min motar na wurin gyara, kawai zan hau taxi ne." Girgiza kai yayi yace "Haba uwata, idan ma baki kira Abbanmu ya zo ya kaiki ba, to mu miye anfaninmu? Muje na sauke ki kawai dama bacci na zo yi." Murmushi tayi tace "Nagode." Zagayawa tayi ta sauke goyon ta bud'a ta shiga, suna tafe suna d'an tab'a hira tana nuna mishi gidan har ya sauke ta, juyawa yayi ya koma ita ta shige ciki. Hanyarshi ta dawowa ne ya hangi Amie kan moto, duniyanci sai abinda ya ci gaba bawai ya rage ba, tsayar da ita yayi suka tsallaka titi suka tsaya, kallon juna sukayi sosai har yau yana tuna Ummy ta fad'a mishi wai Amie ce ta fad'awa marigayiya Shureim d'ansa ne, saida ya fito daga motar ya tsaya gabanta tana fad'in "Mai kyau ya kake? Kwana biyu?" Kallon fuskarta yake da tasha kujera kamar an watsa takin gona yace "Da dama? Ya harkokin?" "Da dama." Ita ma ta fad'a tana d'an sakin kan moton, ba tare daya daina kallonta ba yace "Me ya had'aki da k'awarki?" Kallonshi tayi ita ma tace "Wace k'awar tawa?" "Matata mana, kankana." Wani kallon rashin mutumci ta masa tace "Ba komai, me ka gani?" Murmushi yayi yace "Ko yaron yasan da komai, yaushe rabon dana ganku tare? Sannan har akayi bikinta aka gama ban ganki ba." Cikin rashin damuwa tace "Hakane, kasan duniya juyi juyi ce, k'awance ma yana da tsuntsun soyayya, yau ya hau kanka gobe ya tashi ya koma kan wata." Murmushi ya sake yi yace "Hakane, amma haka yafi faruwa kan k'awancen da ba'a gina dan Allah ba." Tab'e baki tayi tace "Ok, ni zan tafi dan ina da abunyi sosai a gabana." Wani kallo ya mata yace "Ba damuwa, amma idan kin samu dama kije ki ci abincin amaryata." Saida ta kashe masa ido tace "Zan zo, amma ka fara saka min lambarka ta yanda zan sanar da kai zuwan nawa idan na tashi zuwa." Ta k'arashe da mik'o masa wayarta, saida ya kalleta kallo na fahimta sannan ya karb'i wayar, saka mata lambar yayi ya mik'a mata, karb'a tayi tana tana kallon lambar tace "Kai babba ne, lambarka sauk'in hardacewa gareta kamar shan ruwa." Murmushi ya mata yace "Amma ai kinsan ruwa kala kala ne ko, sannan idan ka shanye ruwanka a duniya ko a cikin tekun maliya kake ba zaka iya had'a ko d'igo d'aya ba." Ko da ya fad'a ya wuce abinshi ya barta nan, kai tsaye gidan ya koma ya nufi b'angaren amaryarshi, amma daya shiga k'ofar rufe bai same ta ba, kuma gashi ba zai iya baccin ba idan bata kusa dashi, a hankali ya fito ya nufi b'angarensu Ummy. *Da* sallama a bakinshi ya shiga wanda yayi daidai da fitowar Hamna daga madafa da plate a hannunta da Ummy da Soueiba bayanta da alama aiki suka gama, tana ganinshi ita tasan meya kawoshi gida wannan lokacin, da sauri ta ratsa tsakanin Ummy da Soueiba zata koma madafa ta b'uya, da sauri yace "Algunguma na ganki, maza zo wuce mu tafi to." Juyowa tayi tana turo baki tace "Ba zan je ba ka tafiyarka." Nuna kanshi yayi da yatsa yace "Ni ne kike fad'a ma ba zaki zo ba? Ni kankana?" Lab'ewa tayi bayan Ummy ta rik'eta da hannun d'ayan tana lek'enshi, tunkarowa ya fara yi yana fad'in "Zaki san wa kika fad'awa ba zaki zo ba kankana, ba dai ni ne kika ce ma ba zaki zo ba? Ni ga sakarai ko?" Sake rirrik'e Ummy tayi tana ihu tana fad'in "Ummy ki ce masa ya tafiyarsa, dukana zaiyi." A hankali Ummy tace "Hamna, ke dai kinsan halin kayanki, dan Allah rufa masa asiri ki jashi ku tafi, ke kinsan yanda zaki bashi hak'uri." Kamar zatayi kuka tace "Ummy ni ba zan je gaskiya na gaji." Rik'e baki Soueiba tayi tana kallonta Ummy ma kallonta tayi, takowa yayi da sauri hakan yasa ta dakawa da gudu madafar ta shige, kafin ta mayar da k'ofar ta rufe ya shige ciki, kallon juna sukayi inda Ummy ta girgiza kai tace "Muje Soueiba, ta fito da kuka yanzun, anjima kuma sun shigo nan suna dariya." Dariya Soueiba tayi ta juya zata wuce d'akinta, ihunta sukaji yasa duk suka juya dan ganin me ye? Abun mamaki ganinshi sukayi ya mata dokin wuya ya d'aukota, wutsil wutsil ta shiga yi da k'afafu tana ihu da kwaroroton kiran Ummy tasa ya sauke ta, Ummy ita dariya ma ta shiga yi har da rik'e ciki, ita kam da take ganin kamar zata fad'o ihun ta ci gaba da yi iya k'arfinta, mai gadi da yaji kuwar saida ya d'an lek'o, ko da ya ga soyayya ce saiya koma yayi gum, daya shiga b'angarensu ma saida su Jamila da Farisa suka lek'o, Umaimah ko ko a jikinta dan ba sabon abu bane, tunda akayi aurensu abinda ke faruwa kenan, wani abun ya baka takaici wani ya baka haushi, wani kuma saiya baka dariya har cikinka ya k'ulle, wani kuma in sukayi shi sai su matuk'ar birgeka ka gane cewa akwai fahimta sosai a tsakaninsu, kowa yasan kowa babu mai bawa wani wahala. Sai kan gado ya direta yana b'alle mab'allan rigarshi yana fad'in "Hamna ba ni ne na ce ki zo kika ce k'in ki ba? Zaki ga ikon Allah yau wallahi sai kin haifi yan uku ko na barki." Cikin kuka tace "Kayi na ce to ba zan sake ba, Allah na maka alk'awari." Dungurar mata kai yayi yace "Ke tafi can alk'awarinki na banza, kullum ba haka kike ba." Kallonshi tayi idonshi sunyi launin ja alamar fitina, gashi ta jawa kanta zai murk'esheta da rana patsal patsal, in tayi wasa yau ma sai an mata sabon d'inki, dan yanzu indai ta mishi iskanci to tana nan yake horonta, dan ta samu lafiyarshi sai kawai ta tashi zaune ta shiga cire d'amararshi, yana kallonta ya ga me zatayi sai gani yayi ta fito da...bata tsaya komai ta ba mata masauki a bakinta. Da sauri ya rintse ido ya k'amk'ameta tare da danna kanta yana sauke wani wahalallen numfashi...😎 *Bayan awa biyu* kanshi na kwance tsakanin mamanta biyu, shafa kanshi take a hankali idonta rufe tana ji kamar ita ma tayi k'undubala tace tana son shi, yanda hannunshi ke mammatsa mazaunanta yasa take ta sauke numfashi, dukansu babu mai magana sunyi shiru suna jin dad'in yanayin, wayarshi ce tayi k'ara dake kusa da Hamna kan gadon a cikin aljihunshi, ba tare daya d'ago ba yace "Duba kiga." Hannu tasa ta fito da ita ta duba tace "Babu suna." Hannu ya zura ya karb'a ya danna ya sata a speaker ya d'ora wayar kan cikinta yana saurare, cikin wata irin muryar bariki ta d'aukar hankali aka ce "Hello mai kyau." Ba tare da damuwa ko tunanin komai ba a kasalance ya amsa da "Ya kike? Har kin shirya zuwa ne?" A hankali ta amsa da "Eh, zan zo anjima, me zaka tanadar min?" "Me kike?" Ya fad'a idonshi rufe, cikin kashe murya tace "Kai, kai kad'ai ma ka ishe ni." Ido rufe yace "Na miki yawa, ki dai canza wani abun." Saida ta sake kashe murya tace "Ni kai d'in kawai nake so, in kuma ba zan samu ba nayi zamana." Yana shirin cewa eh tayi zamanta kawai yaji Hamna ta mishi wata hankad'ar tsiya wacce baisan da zatayi hakan ba ya fad'i k'asa kwance, tashi tayi da k'arfi tare da rik'e wayar a hannunta, saida ta sauka daga kan gadon ta d'aga wayar iya k'arfinta ta b'arsata k'asa, fashewa tayi inda ta kalleshi rai a b'ace cikin fitar hayyaci tace "Ni zaka raina Ammar? Me ka d'auke ni nima? Karuwar kamar ta? To baka isa ba wallahi, banyi wannan lalacewar ba." Da sauri ta bud'a kayanta ta zago doguwar riga ta zura ta d'auki hijabi ta saka, ta juyo zata fita ta ganshi yana mayar da kayanshi shima, saida ta harare shi sama da k'asa taja tsaki tace "Na bar maka gidanka ka d'auko duk wacce kake so ku zauna tare." Da sauri ta fita inda ya bita da gudu yana kiran "Hamna, Hamna tsaya ki saurare ni, Hamna dake nake magana." Juyowa tayi a hassale tace "Je veux te tué." Wucewa tayi ta bar d'akin sai b'angarensu Ummy, kai tsaye d'akin Ummy ta shige ta same ta zaune ta idar da sallah la'asar, fad'awa tayi kan k'afafunta ta fashe da kuka, Ummy da gabanta ya shiga fad'uwa da sauri ta aje carbin hannunta tace "Hamna lafiya? Me ya faru kike kuka? Dukanki yayi?" D'agowa tayi abun tausayi tace "Ummy ba gwara ma ace dukana ne yayi ba da abinda ya min, da dukana Ummy ko ji ba zakiyi bare har na zo na d'aga miki hankali." "To meya faru?" Ummy ta fad'a hankalinta a tashe, cikin kukan tace "Ummy yah Ammar baya k'aunata baya so na ko kad'an, Ummy a gabana yake hira da K'awata yar iskan nan Amie, wallahi Ummy ita ce na gane muryarta kuma ita kad'ai ke kiranshi da mai kyau, Ummy yah Ammar ya gama dani a rayuwa." Ajiyar zuciya Ummy ta sauke, sai yanzu ta fahimci al'amarin wato na kishi ne, d'an jinjina kai tayi ta juyo da fuskarta suna kallon juna cikin nutsuwa tace "Me ye tsakaninshi da Amien?" Cikin hushi tace "To ni ina na sani, kawai suna son tozartani ne, Ummy yarinyar fa yar iska ce wallahi ta sawa a gaba, baki ga nima na daina kulata ba saboda ba mutuniyar kirki bace." Kallon fahimta ta mata tace "To yanzu yana ina shi?" Saida ta turo baki tace "Yana can na baro mishi gidanshi." Zaro ido Ummy tayi tace "Kin baro masa gidansa? Hamna me kike nufi?" Saida tayi k'asa da kanta tace "Ni ba zan koma ba." Lallai ta yarda tana son Hamna fiye da yanda take son 'ya'yan data haifa a cikinta, musamman da yar uwarta ma ta mutu saita k'ara ninka soyayyar, amma a yanzu da ake magana kan gidan aurenta, dokenta ta nusar da ita ta kuma nuna mata ita uwa ce, wannan karan ba zata goyi bayanta ba kamar yanda take yi kullum, dan haka ta kalleta tace "Kenan ki ce yaji ne kikayi?" Cikin zumud'i tace "Eh Ummy." Wata tsawa Ummy ta mata da bata tab'a mata ko kamar ta ba tace "Dallah malama tashi anan." Saida ta zabura ta kalli Ummy da mamaki, mik'ewa tayi jiki na rawa tana kallon Ummyn da ita ma take tashi tsaye, kallonta tayi ita ma tace "Kina nufin yaji ne kika min nan? Hamna mahaukaciyar ina ce ke? Auren naki duka yau kwana ashirin da uku ki ce min wai yaji kikayi? To maza wuce koma gidanki." Hannu tasa ta shiga murza ido tana kuka tace "Ummy yanzu ko kiranshi ba zakayi ki tambaye shi me ye tsakaninshi da ita ba? Ni wallahi ba zan iya zama dashi ba indai yana tare da wannan tsinanniyar, haka kawai yaje ya jawo min jarfa." Ita kam dariya ma ta so bata amma saita gimtse fuska, inta fahimta ita ma kamar ta fara son shi kenan, sai dai kuma tana da gaskiya tunda tafi kowa sanin wacece k'awarta ta, dan haka tace "Zo nan." Saida ta tsaya gabanta tana ta share ido ko hawayen babu Ummy tace "Zan kira shi naji me ya faru, amma idan ya fiki gaskiya Hamna dole zaki koma d'akinki, ba zan yarda kullum ana cewa ni ke d'aure miki gindi kina abinda kika ga dama ba, kin yarda?" Turo baki tayi tace "Na yarda." Jinjina kai tayi tace "Shikenan to, mik'o min wayata." Kan gadon ta nufa inda ta nuna mata ta d'auko wayar ta bata, ban d'aki ta shiga dan tsarkake kanta ta samu tayi sallah. Bata kai ga danna kiran ba ya shigo d'akin kamar wani ne ya turo shi daga baya, d'aga kai tayi tana kallonshi kallo na fahimta, duk a hargitse yake hatta kayan jikinshi ma. Shi kanshi tunda tace wai na bar maka gidanka tasa yaji kamar ta soka mishi mashi, kai shi fa wallahi tallahi idan ta sake maganar zata rabu dashi saiya zaro harshenta ya datsashi biyu, ta yanda gobe ba zata sake fad'in haka ba, yo inba ta raina shi ba kan wata yar iska da bata san ma akan me ake magana ba zata fad'a masa hakanen, da marinshi tayi duk da yafi mishi sauk'i kan tahowarta, yanzun haka ya zo ne da niyyar indai zata koma tare dashi to zai durk'usa har gabanta ma ya bata hak'uri, abune da bai tab'a jin ko tsammanin zai ji shi akan wata hallita ba, zuciyarshi ma saida yaji wani zazzab'i ya kamata. Da sauri ya matso kusan Ummy da nufin tambayarta ina take? Rik'e hannayenta yayi zaiyi magana Hamna ta fito da towel d'in Ummy d'aure da kuma d'an k'arami ta d'aure kanta dashi, tana ganin ta juya zata koma da wani saurin bala'i yasha gabanta, kallonshi tayi fuskarta a had'e shi ma kuma haka. Saida ya furzar da iska ya saisaita numfashin shi dake jin kamar zai bar gangar jikinshi kafin yace "... *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:39 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _74_ "Uban waye yace ki fasa min waya?" Wani kallon mamaki ta mishi, wayar shi ma yake magana akai? Sake had'e fuska tayi tace "An fasa d'in, me zakayi?" Rik'e k'ugu yayi yace "Biya na zakiyi ko kuma jikinki ya fad'a miki." Tab'e baki tayi ta rab'ashi zata wuce ya sake tare ta yace "Sai fa kin biya ni yarinya." A hassale tace "Kai kasan ni ba matsiyaciya bace, amma ba zan biyaka ba dan kaji dad'in kiran wasu yan iska kana hira dasu." Da wani mamaki a fuskarshi yace "Iyeee Hamna, ni ne d'an iskan ko yan matan?" Sama da k'asa ta harare shi ta juyo ta tsaya gaban gadon Ummy, bayanta ya tsaya yace "Allah sai kin biya ni kud'in wayata, na yafe miki sauran ma ki ban d'ari biyu, sauran babanki zai cika min." Juyowa tayi tace "Saboda shine ya fasa wayar? To ko ni dana fasa ba zan biya ba." Gashinta dake jik'e da ruwa ya fizgo da k'arfi ya matso da ita kusanshi, k'ara ta saki sanda ya rik'e gashin nata, rik'e hannunshi tayi tana kallon fuskarshi da ido jawur tana shirin yin kuka tace "Sake ni Ammar." Jinjiga kan yayi yace "Waye Ammar d'in?" Da k'arfinta tace "Kai, kai ne Ammar, Ammar Ammar Ammar! Na fad'a sunanka ne ai." Sakin gashinta yayi ya jawo k'ugunta ya had'e da na shi yana mata wani kallo mai ma'anoni yace "Naji zan yafe miki kud'in, amma sai munje b'angarenmu." Hannu biyu tasa ta ture shi tace "Da wa? Ni? Har abada Ammar, wallahi sai ka..." Leb'enta na k'asa yayi saurin cab'owa da yatsunshi biyu cikin tsananin tashin hankali yace "Karki yarda bakinki ya sake fad'in ba zaki koma gida na ba, tawa ce ke har abada, kin gane?" Idonshi ta kalla tana sako da hawaye masu zafi tana fad'in "In dai har kana kula irinsu Amie, to ba gidanka ba kad'ai har da tsanarka saina koyawa kaina, zan tsaneka Ammar tsana ta har abada." Da sauri ya saketa yana sunkuyar da kanshi, hannu d'aya yasa yana murza fuskarshi yana sauke huci mai zafin gaske, kallonta yayi kallo na basira yace "Babu komai tsakani na da ita Hamna, yau na had'u da ita kuma a yau na bata lambata, amma sam ba abinda kike tunani bane." Da k'arfi ta tureshi baya tana fad'in "To miye inba haka ba? Akan me zaka bata lambarka? Me take da shi a jiki dani bana da shi?" Da sauri ya rik'e hannayenta yace "Babu Hamna, bata da komai da yake birge ni ma, ke kad'ai ce ke birge ni a yanzu, bayan ke wallahi babu kowa a gabana." "Amm.." Da sauri Ummy dake tsaye ta zuba tagumi tana kallonsu, kanta har ya fara ciwo saboda cacar bakin nan (ni ma yanzu haka nawa kan ciwo yake Ummy, tunanin yaranki kad'ai nasa gabana ya fad'i), mamakin yanda suka manta da ita a d'akin suke ta maganarsu ma take, wani na fad'a wani ke d'auka shi ma ya fad'a, ita sun hanata damar fad'an wani abu ma, nuna musu k'asan gadon tayi tace "Ku zauna." Kallon Hamna yayi saida ta zauna k'asan tana rufe kafad'unta da k'aramin towel d'in kafin shi ma ya zauna yana ta kallon fuskarta, kan gadon Ummy ta zauna ta kalle shi a nutse tace "Me ya had'aka da k'awarta har ka bata lambarka?" Zunbur ya sake gyara zama kamar mai zaman tahiya yana fad'in "Ummy yarinyar nan bata da hankali karki saurare ta, na kai uwa Zeituna wajen bikin Jumare, na dawo shine na ganta na tsaya muka gaisa..." Duk abinda ya faru ya fad'awa Ummy kafin ya kalli Hamna yace "Shine dan ubanta ta fasa min wayata sabuwa, Allah sai kin biyani ko kuma na siyar da motarki." Nuna shi tayi da yatsa tace "Kar sake zagar min uba malam, ya isheka haka fa." Dafe k'irji yayi da hannu ya zaro ido yace "Lah na shiga uku, Hamna ni kike nunawa da yatsa? Mijinki ne ni fa." Hararanshi tayi tace "Ka sake zagina ma sai kaji tafi a fuskarka Allah." Ummy ya kalla yace "Shikenan Ummy 'yarki wuta zata shiga." Cikin juya baki tace "Sai ka kaini ai tunda kai ke da wutar." Kallonshi Ummy tayi, wai fa so yake ta koma a hakan har ya fara jigata shi, amma dai nuna tsananin damuwar da kuma lallab'ata shine baisan ya zaiyi ba, har da zagi yake had'awa, to a hakan zata koma ko me yake nufi? Had'e fuska tayi ita ma tace "Taje ta fasa wayar, to bari kaji ba ita ba ko ni naga ubanka na waya da wata Allah bayan na fasa wayar ma saina fasa mishi kai, ai kai ta maka mai sauk'i ma, malam fitar min a d'aki." Galala ya kalli Ummy, me take nufi? Ganin baiyi niyar mik'ewa ba yasa Ummy kallon Hamna tace "Yar albarka tashi canza kayanki, zanje da kaina na d'auko miki kayanki adadin da kike buk'ata." Wata dariya ya shek'e da ita yana mik'ewa tsaye yace "Eh lallai Ummy ba zaki iya zama alk'aliya ba, kuma da nasan wariyar da zaki min kenan da ban kai uwata wajen bikin nan ba har sai an gama wannan yak'in." Mik'ewa tayi ita ma ta ja rigarshi tana fad'in "Muje waje a barta ta huta, saina bata maganin ciwon kai tasha saboda damuwar nan daka saka mata." Juyowa yayi ya kalleta yace "Ke yanzu zaki iya zama babu ni a kusa dake? Kinfa san abinda nake baki kina ci cikin dare." Ita kanta Hamna saida ta dara tace "Bana so, ka ci kayanka kai kad'ai." Tsaye yayi ya rik'e k'ugu yace "Ummy kin kassara min zuciyata wallahi, zan fita yanzu amma ba zan sake dawowa nemanta ba, amma Ummy ki tabbatar kin ware mata gadonta, dan zan dinga kawo mata ziyara." Kallonshi tayi tace "To bismillah kaga yanda zanyi da kai." Saida ya kai k'ofa ya juyo ya kalleta yace "An dake ni kuma an hanani kuma, ke dai baki da imani wallahi ko kad'an." Ummy ce tace "Zama da kai ne yasa ta rasa nata ita ma." Ko da ya shigo da dare da sabuwar waya ya saka layikan nashi a ciki, yana zaune yana duba sak'onnin dake shigo mishi ta WhatsApp yaga bak'uwar lamba ta turo mishi hotuna, shiga yayi dan ganin wanene, tashin hankali sanda ya bud'a hotunan, Amie ta turo mishi hotunan ta tsirara, wanda ke da kayan ma kamar ba'a saka ba na d'aukar hankali ne, da sauri ya lik'e idonshi yana fad'in "Ya salam." Bud'ewa yayi ya shiga ya goge su duka tare da bloquén d'in lambar, kiran lambar yayi ko da ta gani ta d'auka jiki na rawa, na yan Maradi ya mata ta hanyar cewa "Ke dan mai... me kike nufi da ni? Na miki kama da d'an iska irinki? To saurare ni da kyau kiji." Saida ya gyara zama yace "In kika k'ara kula ni ma ko a hanya wallahi daga ubanki har kakanki na ashirin sai sun zubar da hawaye, in kika k'ara tuna ko sunan matata ma sai yan uwanki sunyi nadamar kasancewarsu yan uwanki, In kuma kika sake aiko min hoton rub'abb'ar fuskar nan taki mai kama da gurb'ataccen tumatir Allah saina watsa miki asid kin k'arasa dahuwa, shegiya b'abb'akar banza ke ba kyau ba ba kyan jiki ba har ki tsaya kina bariki, to ki kiyaye ni kafin ki fara nadamar sani na da kikayi, yanzu ma wallahi na raga miki ne dan ni dan ni fad'a da mace ba aikina bane, amma da namiji ce ke da tuni na nemi inda kike na cire miki k'ashin baya, 'yar banza mai kama da agwaluma." *Kuyi hak'uri da jaruminku, bakin ya saba da...* Amie da tunda ya fara magana tayi shiru take saurarenshi, saida taji ya kashe wayar ta bi wayar da kallo, ya ci mutumcinta sosai fa ta yanda ba zata iya mantawa ba, amma ya zatayi daya wuce tayi wuri ta aje shi, dan tasha jin labarinshi wurin Hamna tun kafin su b'ata, tasan in tace ma tayi dashi ita ce a kasa da cizon yatsa. Ko da ya gama fad'a shima ya aje wayar ya mik'e ya shiga wanka, daya fito shiryawa yayi cikin kayan bacci ya fesa turare ya fice wajen matarshi. Da sallama ya shiga ya same su duk zaune a falon, kusan Hajia ya zauna yana kallon Nazifa dake kusa da Hamna suna kallon waya yace "Ke tashi samo min abinci." Mik'ewa tayi a ladabce ta shiga madafa, kallon Hajia yayi yace "Hajia jikar nan taki bata san meye miji ba, kiga fa babu ruwanta da na ci abinci ko ban ci ba, ita dai data samu ta cika tunbi shikenan ni na mutu dan yunwa." Ko kallonshi ba bare ta tanka masa, haka ma Hajia bakinta taja tayi gum, jin babu wanda ya kula shi yasa yace "Hajia yau wace rana?" Kallonshi tayi tace "Yau talata." "To juma'a insha Allahu zamu koma sabon gidanmu." Duk yayi maganar ne yana kallon Hamna, duk da bata kalleshi ba shiru tayi daga danna wayarta, sanda tayi k'ok'arin kallonshi kuma saita lura da wajenta yake kallo, dan haka bata yarda ta kalleshi ba, Ummy ma kallonshi tayi ba tace komai ba sai Hajia da tace "Ammar da gaske kake?" A lokacin Nazifa ta fito ta sunkuya ta mik'o mishi abincin, saida ya karb'a ya fara ci yace"Allah kuwa Hajiata, tafiya zanyi daga nan mu barku ku sarara kuma." Cike da rashin jin dad'i tace "Ammar bana so ku bar nan wallahi, in na bari kuka tafi kamar ban cika burin marigayi ba na son zama a waje d'aya, kuma kaga yanzu kana tashi daga nan sauran ma zasu ce zasu tashi." Gyara zama yayi yana kallonta yace "Hajia kiyi hak'uri dan Allah ku ba kowa dama ya d'an matsa, ni na miki alk'awari zumuncinmu ba zai lalace ba sanadiyar tashinmu, na kuma miki alk'awarin ko da na tashi daga nan kullum zan dinga zuwa kowace safiya ina gaishe ki, haka ma kafin na kwanta saina tabbatar da na zo kin ganni na ganki sannan." D'an lab'e baki tayi tace "Shikenan, Allah yasa alkairi." Su Ameer ya kalla dake kewaye da Husseina tana musu tatsuniya ya kalla yace "Heyy, duk wani wanda yasan mallaki na ne shi ya had'a kwomantsanshi, dan babu wanda zan bari." Murmushi ta saki daga nan zaune dan ta fahimci ina zancen ina ya nufa, har ya gama cin abinci suna ta hira dasu Husseina da Hajia, bayin Allah dariya har rik'e ciki sukeyi, sun daddage sai biye mishi suke yi kam, idan ya fad'i wani abu ita kanta Hamna da Ummy sai sun murmusa ko har ma su dara, amma duk da haka bata kalleshi ba bare ta mishi magana. Saida dare yayi sosai kowa yayi haramar nufa inda zai kwantar da hak'ark'arinshi, ta mik'e ta nufi d'akinta na yan mata wanda Nazifa ce a ciki yanzu da Huda shima ya bi bayanta, tsayawa tayi ta juyo ta kalleshi tace "Ya dai kake biyata malam?" Wani kallo ya mata yace "Ke kike bina ko ni ke binki?" Girgiza kai kawai tayi ta wuce, ko da suka shiga suka same su kwance kan gado d'aya Huda har ta fara bacci, wucewa yayi ya kwanta kan gadon Hamna, kallonshi tayi da mamaki cikin rad'a tace "Meye haka malam? Baka ga yara ne?" Rintse ido yayi yace "Ban gansu ba." Juyawa tayi ta kallesu sai taga Nazifa ta mik'e zata fita, da sauri tace "Ke dawo kwanta wajenki, ina zakije ke da nan ne wajen baccinki, bak'on daya mana haure shine zai fita." Ko da ta fad'a ta shige ban d'aki da kayan baccinta a hannu, da murmushi ya bita ya kalli Nazifada ta dawo ko ta koma ta kwanta, bata jima ba ta fito ta aje kayan data canza kan kujera, kan gadon da suke kwance taje ta shige tsakiyarsu tana fad'in "Ku matsa min nima." Bud'a ido Huda tayi ta kalleta ta hangi gadonta, saida gabanta ya fad'i ganin tonton d'in ta kan gadon a dakinsu, juya baya tayi ta yanda take kallon k'ofar shigowa ta matsa mata, wajen k'afafunsu ta maido kanta ta d'ora matashi ta kwanta, ta lik'e ido taji muryarshi tsaye a kanta yace "Ku matsa min nima." A tsorace suka tashi zaune tare ban da Hamna data san halin kayanta, kallonshi sukayi ya kuwa tsaya kusan kanta rik'e da pillow shi ma, Nazifa ce tayi saurin wuntsilawa ta sauka daga gadon ta nufi hanyar fita, da sauri Huda ta tashi ita ma ta bi bayanta suka fice Nazifa na fad'in "Yau mun shiga uku, to su kna d'akinsu wai?" Cikin turo baki Huda tace "Muje d'akin Hajia kawai mu kwanta." Ko da taga sun fita ta mik'e ita ma da niyyar bin bayansu, da k'arfi yayi tsalle ya fad'a kanta hakan ya tilasta mata fad'awa kan gadon da k'arfi, da k'arfi tace "Aouch." Kafin ta bud'a ido taji yayi kwance kanta gaba d'ayanshi ya kuma sakar mata nauyinshi, yanda ya tausheta yasa ta kasa yin numfashi mai kyau, bud'a ido tayi ta kalleshi tace "D'aga ni." Girgiza kai yayi yace "Zaki koma d'akinmu?" Girgiza kai ita ma tayi tace "A'a, har sai na yarda babu komai tsakaninka da Amie." Da k'arfi yace "Babu komai kankana, taya kike tsammanin zanyi iskanci a waje bayan ina da ke? Sannan na rasa da wanda zanyi iskancin ma sai k'awar ki? Na yarda ni mahaukaci ne kuma ba mutumin kirki ba, amma bana neman mata Hamna kuma bana shan ko da sigari bare k'waya." K'afeshi tayi da ido tana kallo, kallon tausayi da jin k'ai da rahama, wa yace shi mahaukaci ne? Dan tana fad'a masa haka ai kawai tana fad'a ne, me yasa zai yarda shi mahaukaci ne kuma ba mutumin kirki ba? Bata ji dad'in abinda ya fad'a ba, a hankali cikin fitar da wahalallen numfashi tace "Wa yace kai ba mutumin kirki bane?" Saida ya k'ank'ance idonshi yace "Ke mana, haka kike kallona ai." A hankali ta d'aga hannunta ta shiga shafa fuskarshi a hankali tana kallonshi, cikin taushin murya sosai tace "Kai mutumin kirki ne Abban yarana, duk gidan nan muna alfahari da kai, dalilinka ne abubuwa dayawa suka canza, ka daina wa kanka wannan kallon, kaji? Ka daina bana so." Yanda ta k'arashe maganar da matuk'ar shagwab'a da kashe murya yasa shi jin zuciyarshi ta k'ara narkewa, murmushi ya saki yace "Amma duk da haka ai baku sona." Idonshi ta kalla tace "Waya fad'a maka, muna sonka yah Ammar, muna k'aunarka dukanmu." D'aya hannun tasa ta tallabo fuskarshi suna kallon juna sosai tace "Ammar *ina sonka*, d'azu nayi niyyar fad'a maka haka, amma wannan Amien..." Ture shi tayi daga jikinta ta tashi zaune tana kallonshi, shi ma kallonta yake yana jin kamar ya fasa ihu yau Hamna ce tace tana son shi? Yana kallonta ta tashi tsaye tana fad'in "Saina fara cin uwar yarinyar nan kafin hankali na zai kwanta, sai naji abinda ya had'ata da mijina." Tasowa yayi yana k'arewa fuskarta kallo yana fad'in "Hamna ni kike kira mijinki? Wuuuuu duniya dad'i, Hamna yau nine kike so? Kishi na kike?" Da sauri ya d'auki wayarta dake kan kujera ya bud'e ya shiga danne danne, tana kallonshi ita dai sai ji tayi ya saka wak'ar *Umar m Shareed* mai taken *soyayya akwai dad'i*, aje wayar yayi sai kuwa ya shiga kwasar rawa ba kunya ba tsoron Allah, da fari da mamaki ta fara kallon yanda yake rawar, amma sai abun ya fara bata dariya, zaune tayi bakin gadon tana kallonshi, tsakaninshi da Allah yake rawar kamar ya ga *Adam A. zango* a gari, bata ankara ba taji ya jawota yana juyata a dole ita ma tayi rawar. Tun tana tirjewa tana so ya rabu da ita har wata wak'ar ta shigo wacce ta iya taka rawarta fiye da zaton mai karatu, (in baku manta ba tun a farkon littafin ita d'in gwanar rawa ce da iya shoki😂), biye masa tayi suka shiga rawa har da dariya kamar mahaukata. Ummy da tasan sai sun tsula tsiya tunda taga ya shiga d'akin, kuma a gaban idonta su Nazifa suka fito, ta jima tana k'wank'wasa k'ofar amma basu ji ba, kuma gashi tana jin dariyarsu da sautin kid'a, dan haka kawai ta tura k'ofar ta shiga idonta rufe dan kaucewa mummunan gani, a hankali ta bud'a ido ta hange su sun cake sai kwasar rawa, rik'e baki tayi tace "Inna lilliahi wa'inna ilaihi raju'un." Da sauri suka tsaya suna kallonta, ko da ya ga Ummy ce ya matso yana fad'in "Ummy albishirinki?" Ta d'auka zai ce Hamna ce ke da ciki, sai kawai ta kalleta tace "Hamna wace lalacewar ce kuma wannan? Rawa a daren nan?" Laushi tayi kamar ba ita ba tana k'yabta ido, jinjina kai Ummy tayi tace "To maza d'auki kayanku ku koma b'angarenku kafin ku tara mana aljanu, tunda abun ya zama iskanci, nan kike ta kumbura ke hushi kike ashe d'aurin duniya ne." Langab'e kai tayi tace "Allah Ummy da gaske ne, yanzu ma da zan ga Amie saina tattaka ta." Kallonta Ammar yayi yace "Wai ke ba zaki fita harkar yarinyar nan bane?" Zaburo mishi tayi tace "Eh d'in ba zan fita ba, sai naji dalilin da yasa ta kula ka." Kallon fahimta ya mata yace "Ki tabbatar zaki b'arar min da ita?" Cike da tabbaci tace "Allah kuwa zan iya." Kallonta yayi da kyau yace "Gobe da safe ki shirya idan zan fita na kaiki gidansu, zan so ganin yanda zaki d'auketa ki nunawa sama ta bakwai kafin ki dirota k'asa, dan ni abun farin cikina ne ace matata na fad'a akai na, kinji ko?" Cikin murna tace "Da gaske?" Ba alamar wasa yace "Ina fad'an abinda ba zan iya bane?" Da farin ciki tace "A'a." "Dan haka ki shirya zan kaiki." Ko da ya fad'a ya juya zai fita, ita har ga Allah ta ma manta wai yaji tayi, kallon Ummy tayi tace "Saida safe Ummy." Rik'o hannunta tayi ta dawo da ita baya tana fad'in "Zo nan." Kallon juna suka shiga yi Ummy tace "Hamna ina yace zai kaini? Gidansu Amie fa naji yace." A hankali tace "Eh Ummy." Da mamaki Ummy tace "Anya kuwa Hamna kina so mu zauna lafiya dake? Ke fad'a min me kike so ku zama yanzu?" Shagwab'e fuska tayi tace "To naji Ummy ba zamu je ba." Tab'e baki tayi tace "To yanzu binshi ne zakiyi?" Da sauri ta juya ta nufi kan gadon tana fad'in "A'a Ummy, bacci zanyi." Nufa kanta Ummy tayi tana neman abun bugu tana fad'in "Hamna zan ci ubanki a gidan nan, tashi wuce ki bi mijinki, na gaji da masufarku wallahi karku kashe ni da raina." Da gudu ta arta ta fito daga d'akin, ko sauka bai gama ba daga matakala tayi tsalle da niyyar haye bayanshi, shi kuma da baisan da zuwanta ji kawai yayi yayi sungululu ya tafi ta kai suuuu.😂😂😂😂😂 *Tsakaninku ne* Bashi daya rigata ba har ita san da kai tayi duk suka wuntsile a wurin, saida suka gama durkuwa k'asa suka fara kallon kansu dan ganin salon fad'uwar, Ammar😂 da yaji kamar wuyanshi ya karye kallonta yayi, tana zaune kan matakalar ta rik'e k'afa da hannu tana kukan shagwab'a, wani huci ya shiga saukewa da tunanin me ma zai mata ne shi kam, shin ya d'auke ya jujjuyata sannan ya dasata a k'asa, ko kuma ya sake hawan benen da ita sai ya sakota ta fad'o, ko kuma... *Uwar Lalla ranar da aka kawoni gidana haka na kusa tahowa ta kai na karya wuya😂 amma tuni angona ya cab'oni aradu ta baya, kai bene baiyi ba.* Ummy dake tsinkayensu ta sama tana jiran taga me zai faru, tashi yayi a hassale yana fad'in "Ke dan ubanki ni kika wuntsilo? Hamna ni kikawa wannan wurgowar? Ashe k'arfin tsiya ne dake kamar bagwariya, ai kuwa yau zaki c..." Da sauri Hamna data kasa tashi saboda k'afarta ta bud'e hannayenta ta jawoshi da k'arfi har yana neman fad'awa kanta, bai gusar da fuskarshi daga kanta ba yana mata kallon mamaki yaga ta k'amk'ame shi tana fad'in "K'afata! Wayyo Allah k'afata, yah Ammar ka taimaka min dan Allah." Kallon fuskarta yayi kawai yaji a ranshi ta gama dashi, kallon k'afar yayi wacce ke rufe da dogon wando, sake kallonta yayi yace "Ciwo take miki?" "Eh." Ta fad'a tana rushewa da kukan shak'iyanci, d'aga kai yayi ya kalli Ummy sannan ya kalleta yace "Bari Ummy ta taho saita kaiki d'akinki, ni dai ba zan d'auke ki ba." Da sauri ta k'ara jawo rigarshi tace "A'a d'auke ni, d'aukeni muje b'angarenmu kafin Ummy ta taho, ita ta koro ni fa daga can." Murmushi yayi yace "Allah?" "Eh." Ta fad'a da sauri tana d'aga mishi hannu saiya d'auketa, gyara tsayuwarshi yayi ya d'auketa gaba d'ayanta ya k'arasa sauka da ita, ba tare daya juyo ba yace "Ummy saida safe, yar yajinki ta koma." Rufe fuska tayi cikin k'irjinshi har suka fice, har saida suka b'acewa ganinta sannan ta girgiza kai ta shiga saukowa a hankali tana fad'in "Allah kaine Allah, Allah ka shirya min yaran nan shirin addinin musulinci, Allah ka kawar da idon mak'iya da bakin mutane akan su." *Ameen Ummy.* *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:39 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _75_ Ko da suka shiga ya sauketa kan gado, zaune yayi ya fuskanceta da kyau yace "Hamna, yanzu nan duk cutar nan da kika min shikenan kin cuci banza kenan?" Saida tayi da gaske ta samu ta rik'e dariyarta tace "Rama to." Zaro ido yayi yace "Ni! Ni d'in banza da zan rama, a'a na yafe." Cikin bushewa da dariya tace "To bacci zanyi." "Kwanta." Ya fad'a yana kallon idonta, zanin rufa taja ta rufa tana dariya k'asa k'asa, sai yanzu take hango sanda ta bankad'o shi yayo k'asan nan daram, sai kawai ta juyo tana k'ara barkewa da dariya, ganin tana dariyar ba tsayawa har da rik'e ciki yasa yace "In ban miki Allah ya isa ba ki ce ba sunana Ammar ba." D'aga mishi hannu tayi alamar ta daina tare da rufe bakinta tana wata dariyar, shi dai har bacci ya d'aukeshi bai tanka mata ba tana dariya. *Ko da* suka gama kari zai fita yace su tafi ya kaita, kallonshi tayi tace "Wai da gaske kake dama?" Ba alamar wasa a tare dashi yace "Ina wasa dake ne?" "A'a." Ta girgiza kai a hankali, d'orawa yayi da "Zaki tafi ko na tafiya ta?" Cikin turo baki tace "Gaskiya ka tafi, Ummy tace zanga b'acin ranta." Wani kallo ya mata na tsanake, shi fa akwai abinda yake nufi daya fad'i haka, in bata amince ba kuma akwai matsala, amma cikin ruwan sanyi zai bita sai kawai ya juya yana fita yace "Shikenan, saina dawo, amma kar kiyi mana abinci yau zamu fita waje." K'ala ba tace ba har ya fice. *An shirya* dan fita kamar yanda yace, amma sanda ta fito cikin shirin riga da siket d'inta da mayafi saiya shiga zagayata, tsaye tayi tana binshi da kallon kafin ya tsaya gabanta yace "Yanzu Hamna dan zamu fita shine sai kin fad'a ma kowa cewa gaki nan kin fito." Da mamaki tace "Kamar ya fa?" Saida ya nuna kamar yana ganinshi yace "Shi wannan turaren da kika fesa fa?" Yar ajiyar zuciya ta sauke tace "Ohh, yana da dad'i ko?" Wata harara ya wurga mata yace "Dad'in banza dad'in wofi, ni ba dad'inshi nake tambaya ba." Kamar wacce ta tuna da wani abu sai kuma tace "Au, sunanshi? Sunan shi *Oud zarkah*, ka gane." Rik'e k'ugu yayi dan ya fahimci zata raina masa hankali ne yace "To je ki cire kayan nan ban son jin k'amshinshi jikinki." A kasalance ta amsa da "Ba fa a kayana bane, a wuya da baya kunne kawai nasa." Cike da raini yace "To je kiyi wanka." A kasalance ta sake amsa shi da "Ko nayi ba zai fita ba, kamu ne dashi." Da hannu ya mata alama yace "Can naga lalle iyakar kamu, je ki wanke min shi Hamna kafin ranki ya b'ace, ko da ruwan gidan nan da garin nan zasu k'are to zan d'ebo miki ruwan maliya dan ki wanke shi." Galala ta kalleshi tace "To da wannan nayi zamana mana, fitar ta zama dole ne?" Saida ya sake rik'e k'ugu gam yace "Qur'ani sai kin tafi." Saida ta waina idonta alamar gajiya da zancen sannan ta juya ta koma ciki, canza kayan tayi ta sake wasu kafin ta fito suka fita. Saida aka d'auki hanya yace ai fa an ma fasa cin abincin, kawai wasu almajirai zasu tsaya wani cin abinci a waje, ji tayi rainin hankalin ma ya wuce misali, k'ufula tayi ta had'e girar sama da k'asa ta rumgume hannaye, saida ya samu wurin da babu hayaniya ya caka birki ya tsaya, a hankali ya kamo hannunta yana kallon fuskarta yace "Baby, kalle ni nan." Kallonshi tayi amma asali harara ce take masa, kashe murya yayi yace "In tambaye ki mana?" Kafeshi tayi da ido alamar ina saurarenka, saida ya d'an muskuta zamanshi yace "Kina so na da gaske?" Turo baki tayi tace "Me kuma ya kawo wannan maganar yanzu?" "Ki bani amsa." Ya fad'a yana ci gaba da kallonta, juya kanta tayi tace "Eh." Sakin hannunta yayi yana tayar da motar yace "Muje to na siya miki ice cream." Kallonshi kawai tayi ita dai har suka fara tafiya, ta kusan salon d'inta suka bi wanda har ta kalli wajen ta ga a rufe alamar *Lina* har ta rufe, dama ba wata tsiya suke yi ba tunda ta bar zuwa sai jifa jifa, a hankali yake tuk'in zasu wuce ta wata majalisar samari, Hamna da idonta ke kallon hanya da sauri ta rik'o hannunshi da yake tuk'i tace "Lah! yah Ammar dubi mutumin nan da yasa aka daki yah Amar." Saida ta gama fad'a sai kuma ta gane katob'arar da tayi, a hankali ta shiga sakin hannunshi tana jujjuya ido da matse bakinta, cak ya tsayar da motar yana kallonta yace "Yana ina?" Ko kallonshi ba tayi tace "Wanene?" Da k'arfi yace "Ban sani ba? Yana ina na ce?" A tsorace ta kalleshi inda ta ga ranshi ya fara b'acewa zai iya cin ubanta ma, cikin i'ina tace "B..a komai fa, na d'auka shine." Bayan wuyanta ya cakumo da k'arfi ya matso da fuskarta kusanshi cikin daka tsawa yace "Hamna karki b'ata min rai, ki nuna min shi ko na had'a duka wanda ke wurin na taka su da mota." Yanda ya rik'e wuyan nata yasa ta cewa "Zan fad'a maka to, sake ni dan Allah." Sakinta yayi inda ta sake kallon matasan, a hankali ta kalleshi tace "Waccen ne mai jan riga." Kallonshi yayi da kyau, murmushi ya saki ya kalleta tare da jawo kanta ya sumbaci bakinta yace "Ni ma ina sonki." Ture shi tayi tana fad'in "Ni bana son ka." Dariya yayi yace "Baki isa ba yarinya, ko kina so ko baki so dole ki soni, inba haka ba duk zamu mutu tare." Saida suka siyi ice cream d'in ya mayar da ita gida ya aje, sanda ta sauka kallonshi tayi tace "Kai ba zaka shigi bane?" "Kije akwai inda zanje." Ya fad'a yana wucewa a hankali, da kallo ta bishi kafin ta shiga sam bata tunanin me zaiyi. Inda suka bari ya koma ya tsaya, cikin sa'a yana zuwa kuma saurayin ya hau moto zai bar wurin shi da wani, bin bayansu ya shiga yi hankali kwance har ya aje wanda ya d'auko a wani shago yayi gaba, ya shiga layin gidansu kenan yayi gaggawar shiga gabanshi, tsaya yayi da sauri yana kallon motar, bud'ewa yayi ya fito da k'arfi cikin tako mai ban tsoro ya nufi kanshi, shi kam gabanshi ne ya shiga fad'uwa dan yasan akwai matsala, wanda yasa aka daka ne ya dawo d'aukar fansa, gashi shi kad'ai a wurin kuma ko ihu yayi ba za'a iya jinshi a gidansu ba, jiki na rawa ya shiga k'ok'arin sauka daga kan moton. Bai bari ya gama sauka ba, bai bashi damar sauka ba ko da kare kanshi ne yayi, da iya k'arfin da yake da shi ya gabza mishi wani k'ulli a baki, rikicaaaa sukayi shi da moton duk suka fad'i b'angaren hagu, moton ne ya taushe k'afarshi hakan yasa shi kiciniyar jawo k'afar, k'afa yasa ya take moton yasa hannu ya jawo madubin moton da k'arfi, yana cire shi ya gaud'a mishi a fuska a take jini ya sake gabce mishi, shak'o wuyanshi yayi ya kalli idonshi yace "Wai kai ga sakarai, a madadin ka fuskance ni ka rama dukanka, sai ka zagaya ka turawa d'an uwana yara suka dake shi." Sauda ya gaura masa mari yace "Shine har da sawa suka karya mishi hannu." Hannu ya d'aga zai sake marinshi yayi saurin tara hannu yana fad'in "Yi hak'uri, yi hak'uri dan Allah, bansan d'an uwanka bane." A hankali yace "To ka sani daga yau, ni dashi tare muka fito duniya, sannan ina jiranka ka sake aiko min yara yanzu." Dungurar dashi yayi ya juya ya koma mota, saida ya bad'a mishi k'ura ya bar wurin hankali kwance, yanzu kad'ai yaji sakayau daya ramawa d'an uwanshi, shi fa bai son abinda zai tab'a mishi Amar, waccen lokacin ma yayi shiru ne dan baisan mutumin ba. Shi ma saida aka d'aukeshi daga nan akayi asibiti, sai dai al'amarin yayi k'amari sosai, mahaifinshi ranshi ya b'ace sosai ya kuma ce ba zai yarda ba, sai sunyi k'arar shi tunda dai akwai mahukunta a gari, da yake shima d'an dangi ne kuma akwai masu abun hannu sai fa kowa ya goyi da bayan haka, dan haka suka jiran gari ya waye yaji sammaci. *Washe gari* ya shirya ya fita cikin farin ciki, amma fitar da bai dawo gidan ba kenan, motar police ce ta zo har gidan nemansa, mai gadi ya gane wa ake nema da suka fad'a masa yan biyu, domin kuwa yanda sukayi réclamén abun ba da wasa bane, sun d'auka zafi sosai su ma, nan ya fad'a musu yana asibiti suka pantsama can, ganin motar ma da yanda take tafiya saiya kayar da gaban mai tsoro (iri na ba, ai bana son had'uwa dasu ko da croisement ne). A tak'aice dai kunsan halin kayanku ai, bai musu magana da ladabi ko girmamawa ba, su kuma hakan ma sab'a dokarsu ne, dan haka laifinshi ya k'ara girma suka ram da shi😂 (yau maza an shiga hannu aradu, uwar Lalla a shirya kai mishi abinci). Ko a jikinshi ko nace a kwalar rigarshi, binsu yayi babu gardama ko musu ko nadama a tare dashi, sai dai abun ya wuce yanda yayi tunaninshi, dan kai tsaye babban gidan kaso suka wuce dashi, kuma ba'a b'ata lokaci tsayawa tambayarshi wani abu ba, jefashi kawai sukayi ciki suka rufe bayan sun raba shi da wayarshi. Babu wanda hankalinsa bai tashin ba sanda labarin ya riski kowa, Hamna da Hajia ma kuka suka shiga yi, a tsaye lieutenant yaje dan jin abinda ke faruwa? Fad'a, ya daki wani har ya ji masa ciwo yana kwance, sannan ya zagi tenu (ma'aikanta masu kaki) shine abinda aka fad'a mishi, al'amarin bai mishi dad'i ba, ranshi ya b'ace ta yanda ya juya ya tafiyarshi ba tare da yace komai ba, tunaninshi shine akan me Ammar ba zai yarda ya girma ba? Da yaranka har shida amma kana abu kamar yau aka haifeka. Gidan ma daya fad'a musu basu ji dad'i ba, amma su Hajia suka ce ya zasuyi daya wuce hak'uri su fito da shi, Hamna kuma da taji sai ta aza sabon kuka tana fad'in laifinta ne ai, da bata kula saurayin ba duk da haka bata faru ba, sannan da bata nuna mishi shi ba jiya da yanzu yana gida. Nan dai lieutenant da Labaran suka shiga k'ok'arin fito dashi tun kafin ma kowa yasan da al'amarin, amma abun ya wuce yanda suka tunaninshi, dan abu d'aya da aka fad'a musu shine sai an musu sulhu sun ce sun yafe, kafin nan saida suka d'auki nauyin maganin yaron. *A gurguje* *Abu* fa ya ci tura yaja daga, duk abinda aka ce suyi yi sukeyi amma shiru, saida aka kwana *shida* kad'ai aka zauna dan ayi sulhu, mahaifin yaron mai sunan *Ak'il* da yayanshi duk suna tare dashi, sai lieutenant da Labaran da kuma Ammar d'in. Nan aka ce ya bashi hak'uri sannan babu shi babu shiga harkarshi har abada, nan fa ya rantse ya maimaita cewa ba zai bashi hak'uri ba, in ma suna da abunyi suje suyi kar su b'ata lokacinsu, Labaran ya lallab'a ya bashi hak'uri a wuce wurin, durk'usawa wada ba gajiyawa bane, amma yace wannan wanda dai sai dai ya ida takeshi ya shige cikin k'asa. Hakan yasa lieutenant ranshi b'acewa yace su barshi kawai, fita yayi ya bar Labaran yana ta tausarshi, amma abun haushi yaron nan da shegiyar kafiya yace ba fa zai bayar ba, babu yanda za ayi an dakar masa d'an uwa kuma ace ya bayar da hak'uri dan an raina shi, shi ma Labaran haka ya baro wurin rai babu dad'i, su kuma suka ce zasu nuna mishi taurin kai da iskanci, tuni kuga gane shi suka kafa mishi kahon zuk'a. *Daga* lokacin nan kam abubuwa suka canza mishi, ya jigata ya kuma yarda daya fara wahala, amma dai bai yarda ya nuna uban kowa ya gane ba😂 (wuya makarantar kare), abinci da aka kawo masa kullum na safe daban na rana daban na dare daban, amma suma ana kawo shi zasu juye a nasu kwanon su cinye, wanda ake girkawa anan wanda maza ne ke surfa masarar ayi tuwon suke bashi, sai randa sukayi niyya ne suke rage mishi su zuba a leda su jefa mishi, bai tab'a nuna musu komai ba yana kallonsu dai duk ya gane fuskokinsu zaiyi wanka ya canza kayan da aka kawo mishi, amma fa sauro da rashin lafiyayyar shinfid'a da kuma rashin kankana ma kad'ai sun addabe shi, suna tsangwamarsa a wurin da jefa mishi magana, wankin ban d'aki da shara duk babu abinda basa saka shi a wurin, amma duk sanda yake aikin cikin izza da jin kai yake yin shi, ko wayarshi basa bashi kamar yanda suke ba wasu dan suyi kira su maido, sun hana shi ganin kowa kai kace ya saci kud'in gwamnati ko kisan kai, shi kuma ya riga daya san laifinshi bai kai hukuncin da suke mishi ba, shiyasa ma ya zuba musu ido yana k'arewa duk wanda ya masa da kallo, jira yake su gama nasu kafin ya darza musu salon tashi didimar. *Comment...* *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _76_ *Sati biyu* kenan da rufe shi, colonel da gwamna babu mai labari, lieutenant nan ne ya tsawatar kar wanda ya fad'a musu, amma tsakanin mata da miji sai Allah, yau dai abun ya damu Hamna ta yanda take jin ba zata k'ara kwana ba tare da mijinta ba, kiran Gambo tayi tana kuka, yana jin muryarta cikin kukan nan yasa dreba ya tsayar da mota, yana kan hanyar shi ta zuwa aéroport zai bar k'asa ya dakata, cikin tashin hankali da kulawa yace "Hamna me ya faru? Lafiya kike kuka? Me akayi?" Cikin matsanancin kuka tace "Abba sun rufe yah Ammar, kuma Abba ya hanaa fad'a maka, dan Allah Abba ka taimaka ka fito dashi, ba fa wani laifi ya aikata ba." Ajiyar zuciya ya sauke ya rintse ido yace "Me yayi aka rufe shi? Tun yaushe yake rufen ma?" "Abba satin shi biyu?" Da k'arfi cikin razani yace "Me? 2 semaine? Me yasa Hamna? Shin yaron nan baya da gata ne ko me?" Cikin kuka tace "Abba ne ya hana a fad'a maka." Tsaki yayi tare da kashe wayar, kallon dreban yayi yace"Muje." Babban mai tsaron lafiyarsa dake kujerar gaba ya kalla yace "Gida zamu je yanzun, kayi magana da dreban jirgin, ni zan kira président muyi magana." Bai tsaya tambayarshi ba dan in dai kaji yace gida to gidan Hajia yake nufi. A d'an lokacin da bai taka kara ya karya ba suka iso, suna shigowa garin ya kira colonel da a lokacin yake wani k'auye a *mali* ya fad'a mishi tare da neman taimakonshi, wai Allah zo kaji fad'a wajen uban Ammar, yanda kasan Gambo ne mai laifin haka ya dinga kirta masifa ba k'akk'autawa, shi dai bai taya shi ba har ya gama yace yaje gida zai tura mishi da wasu daga cikin sojoji, yo su za'a nunawa kaki, a k'arshe ma cewa yayi kaf jami'an sun ci...har da shi ma bai cire kanshi ba da lieutenant d'in.😂 Da isar shi gidan ko ciki bai shiga ba suma suka k'araso, Hajia kawai ya gaishe da ita yace zai je ya dawo yanzu, daya fito shi kanshi saida gabanshi ya fad'i, to me Hussein ke nufi daya turo wannan motocin, mota har hud'u da sojawa a ciki, duk akan menene? Duk fitowa sukayi suka shiga sara mishi da girmamawa, kafin babban cikinsu ya sanar dashi colonel ne ya turosu su bashi tsaro inda zaije, godiya ya musu kafin suka d'auki hanya, kamar wanda zasu tafi yak'i, shi ga nashi motocin dake ta jiniya wi wi wi, duk inda suka wuce sai an bisu da kallo sai dai zaka san babba ne ya zo. Sanda suka isa, a lokacin da suka shiga wurin da matsiyacin gudu, kafatanin sojojin dake ciki kowa neman bindigarshi yayi ya sake rik'eta da kyau, kowa ya gama zama a ankare dan tunaninsu gari ne babu lafiya, ko ana wani babban fad'a ko kuma wani garin ne ake yak'i aka zo neman taimakonsu, duk sun tsaya cikin shirin kota kwana na tafiya, suna kallo sojojin ke ta durkowa daga cikin motocin, sai dai motar da gwamna ke ciki suka ga garde cord d'in shi ya bud'e yana hakimce bayanshi, da mamaki suka bishi da kallo suka kam, basu san da zuwanshi dan ana d'aukarsu wani lokacin dan su kare lafiyarshi, sai kawai ganinshi sukayi anan, to me ya kawo shi? Tambayar da kowa ya jefi kanshi da ita kenan, yana gaba garde d'inshi na bayanshi da bindigarshi ya d'ora hannu kanta, sai soja biyu a gaban gwamnan wanda suna cikin masu tsaronshi, sai sauran jami'an a bayansu duk suka k'araso wajensu suka tsaya, suma dai gefe sukayi da bindigoginsu suka shiga sarawa duk wanda ke sama dasu, da hannu kawai ya musu alamar su shiga ciki, jiki duk a sab'ule suka rufa masa baya da tunanin ko lafiya? Kujera suka matso mishi da ita ya zauna, amma saiya tokare ya tsaya ya kalli k'aramin major d'in yace "Je veux voir mon fils, je peux?" Gabanshi yayi ya yanke ya fad'i a take ya fara salatin annabi, to waye d'anshi anan gidan? Cikin tsoron al'amarin yace "Pardon g..." Katse shi yayi da cewa "Tout de suite." Wani d'an matashin jami'i ya kalla kafin ya kalli gouverneur d'in yace "Son ...nom?" Cikin muryar gargad'i yace "Ammar Hassan Suley Gaga." Yana kallon k'aramin jami'in yayi sauri ya juya, Gambo ya had'e fuska sosai ya kuma kafe major d'in da ido sai ya d'an jima yake k'yabtawa, shi kuma yayi k'asa da kanshi yasan kallon zaka ci ubanka ne idan aka fito min dashi, jin motsin sun fito yasa shi juyawa dan ya ma k'ara kallon d'an, ko da ya kalleshi a ranshi yace "Wannan sarkin girman kan? To ai shi ya so zama anan." Ko da suka fito ya hangi Gambo sai kuwa Ammar ya tak'ark'are ya d'ora hannaye saman fuska ya shiga murzar ido wai shi a dole kuka ne yake, da sauri Gambo ya k'arasa ya tarbe shi da niyyar rumgume shi, amma ikon Allah sai Ammar ya fad'i k'asa zaune yana kuka cikin babbar murya yana tumurmusa k'afafu yana fad'in "Ni kawai ka koma babu inda zanje, haka kawai kuka manta dani a wurin nan suna ta dukana." Rigarshi mai botira a gaba ya shiga kiciniyar bud'ewa yana fad'in "Dubi yanda suka farfasa min jiki, kamar ba d'anku ba ace duk babu mai so na a cikin, kalle ni fa dan Allah." D'aga kai yayi sama yana wani kukan, kaf wurin babu wanda bai sakar masa ido ba, sai dai Gambo tuni ya harbo jirginshi yasan me yake nufi da abinda yake yi, juyowa yayi ya kalli major kafin yayi magana ya d'an muskuta tsayuwarshi yace "Wallahi yallab'ai babu wanda ya tab'a dukanshi a wurin nan, ko?" Ya tambayi sauran yaran, dukansu girgiza kai sukayi alamar eh, kallonsu yayi ya tsaya da kukanshi yace "Na muku k'arya kenan?" Kallon Gambo yayi yace "Abba na, ina k'arya ne ni?" Juyawa Gambo ya sake yi ya kallesu yayi k'wafa tare da jinjina kai, sunkuyawa yayi ya tallaboshi yana fad'in "Rabu dasu yaro na, ai ba sai ka fad'a ba ma na sani, dubi duk yanda ka lalace." Ai sai yaji dad'i Gambo ya taya b'era b'ari da sauri ya kamo hannunshi suka dawo kusa dasu, uku daga ciki ya nuna yace "Abba wad'an nan suke cinye min abinci na ina ganinsu, sai su had'a ni da wani banzan abinci bana iya cin shi ma, ni kawai ban yarda ba wallahi sai na shigar da k'ararsu." A take suka shiga kallon kallo suna tausayawa kansu, su ai basu san girmanshi ya kai haka ba, kallonshi Gambo yayi yace "A'a bana son maganar shigar da k'ara, amma dai ka fad'i wani abinda kake so ni zan maka." Ai da sauri major d'in yace "Yallab'ai..." Kallonshi yayi yace "Ferme là." Shirun yayi yana kallon Ammar dake kallonsu shima, a hankali yaji yace "Kawai su biyani kud'in abinci na." Saida ya sauke ajiyar zuciya ta jin dad'i, da sauri cikin yaran wani yace "Nawa kake so yallab'ai." Saida ya harare shi yace "Dukanku ku bada jaka sha biyar biyar." D'aya daga ciki ne ya d'an bud'a baki irin yaushe muka ci wannan abincin? Idan siya zamuyi fa jaka goma zata bamu buhun oriba rice, major d'in suka ga yasa hannu aljihu ya ciro kud'in ya mik'a mishi, karb'a yayi tare da tara hannu wa sauran suma, da k'yar suka lalabo kud'in tunda wata yayi nisa😂, kallon major d'in Gambo yayi yace "Ya zamuyi yanzu?" Girgiza kai yayi yace "Yallab'ai comme tu le veux." Kallon Ammar yayi yace "Ina so na koma da yaro na, shin akwai tara ko wani abu ne?" Girgiza kai yayi yace "Tun ranar aka so musu sulhu shine ya k'i." "Me ye abunyi yanzu?" Saida ya d'an kalli Ammar daya kafesu da ido yana ta kallo yana tunanin ta yanda zai diro musu kafin yace "Tara ce zai biya, sai kuma dan Allah ya kiyaye gaba, fad'a ba na shi bane yana babban mutum, sannan ya fita harkar yaron dan iyayenshi sun ce zasu d'auki mummunan mataki idan ya k'ara tab'a musu yaro, shine kawai." Hannu yasa aljihun rigarshi ta ciki ya fito da cash yan jaka goma goma d'auri uku na 300 000 ya ajiye gaban teburin yana fad'in "A biya tarar, insha Allah kuma za'a kiyaye." Kasa amsa mishi major d'in yayi kud'in nan sun gama haukatashi, yana rik'e da hannun Ammar zasu wuce Ammar yace "To wayata fa ko kuna da gadona ne?" Da sauri major d'in ya jawo wani coffre ya fito da wayoyi ya aje gaban tebur d'in, dubawa yayi ya d'auki tashi ya juya zasu tafi, Gambo ne yace "Bayan wayar babu kayanka ne?" Ba tare daya kalleshi ba yace "Me zanyi dasu to? Su d'auka na bar musu." Suna k'arasa aka bud'e musu motar suka shiga tare, saida suka d'auki hanya Gambo ya kalleshi da kyau, yayi bak'i abinki ga jar fata, ya rame sai gashi da duk yayi baje baje ba kyau, a hankali yace "Ammar." Ba tare daya kalleshi ba yace "Na sani Abba, zan daina." Da mamaki ya kalleshi yace "Kasan me?" Yana kallon titi yace "Nasan cewa za kayi na daina rigima na girma, na daina irin wannan abubuwan ni ba yaro bane, sannan idan ban bari dan komai ba na daina ko dan iyalina." A d'an tsorace ya kalleshi ya had'e yawu, har ga Allah abinda zai fad'a kenan, dan ko da kalaman sun banbanta maganar dai d'aya ce, da k'yar ya k'ak'aro murmushi yace "Ka min alk'awarin zaka daina to?" Fuska a had'e yace "Eh Abba." Rik'o hannunshi yayi yace "Nagode, kuma na ji dad'i sosai, kaga su kanka iyalinka hankalinsu zai kwanta." Yar k'aramar k'wafa yayi ya matsu ya ganshi gida ya tashi hankalin uban kowa, ba dai shi suka wofantar ba? Zasu gane yau d'in nan zai bar musu gidan ya koma na shi gidan, har ita kankana sai ta ci kakanta yau, inbai manta ba da aka tab'a rik'e shi marigayiya zuwa tayi tace sai dai su kwana, amma ita shine babu ruwanta ko? Ko da suka zo gida kusan babu wanda ya fita dan safiya ce, a lokacin Hamna tana tare da su Ummy suna shirya teburin cin abinci, suna juyawa dan amsa sallamarsu suka had'a ido, da wani irin farin cikin da ita kanta bata san ta samu kanta a ciki ba ta saki cokalan hannunta ta ruga a guje, ta manta da duk iyayen dake wuri ta fad'a k'irjin mijinta. Saida ya lumshe ido alamar sak'on ya isa inda aka aikashi, amma da yake jaraba ce ya shigo da ita saiya ture ta a jikinshi ya kalli Gambo yana nuna mishi yace "Ka gani ko Abba, lafiyayyen abun kari ne suke shiryawa zasu ci hankali kwance, nan kaga alamar damuwa tare da wani na rishina a gidan?" Kallon Ummy yayi da su Hajia da su lieutenant yace "Du barkanku da warhaka, Allah ya k'ara muku lafiya da arzik'i." Da kanshi kuma ya amsa da "Ameen." Hamna ya kalla kafin ya ankara ya cakumo hannunta ya fita da ita daga d'akin, k'ok'arin k'wacewa ta shiga yi tana fad'in "Yah Ammar, yah Ammar sake ni mana, dan Allah sake ni." Saida suka kai k'ofar d'akinsu ya ja ya tsaya ya kalleta yace "Bud'e min k'ofar." Kamar zata yi kuka tace "Makullin yana can na baro, bara n..." Bata kai k'arshen maganarta ba taga yasa wa k'ofar k'afa da k'arfin sababi ya turata, ba shiri k'ofar ta wangale ta bud'e, turata yayi da k'arfi har tana neman fad'uwa kafin ya shiga shi ma, da sauri ya shige madafa inda ta mik'e dan binshi ta ga me zaiyi, tana kaiwa k'ofar shi kuma zai fito suka had'e, kwanukan data jera a madafar kamar kwalliya ta ga ya fito dasu a hannu, da mamaki ta kalleshi tace "Yah Amm.." Bai bari ta gama fad'a ba ya buga kwanukan a k'asa, masu fashewa kam sun fashe mai lotsawa ya lomatsa, baki bud'e irin abun ya firgitata ta kalle shi tace "Wai me ye haka? Lafiyar ka..." Sam bai bari ta fad'a abinda take son fad'a ba saboda hannun daya d'aga zai gaura mata mari, amma kuma kasawa yayi saiya kafe fuskarta da kallo, tsoro k'arara ne bayyane a fuskarta ta rintse ido ta kawar da kai gefe tana jiran jin saukarshi, jin shirun yasa a hankali ta shiga bud'a ido ta sauke kanshi, suna had'a ido sai kawai ta fashe da kuka dan abinda zata iya yi kenan, tana ganin ya sauke hannunshi k'asa sai kawai ta ruk'umk'umeshi a jiki tana sake fashewa da kukan sosai. K'amk'ame shi tayi sosai tana fad'in "Kayi hak'uri yah Ammar, kayi hak'uri dan Allah kar kayi hushi dani, wallahi Abba ne ya tilasta ni kar na fad'awa kowa, kayi hak'uri dan Allah, yanzu ma nasan na sab'awa Abba tunda na kira Abba na fad'a mishi." Wani irin tausayinta ne ya kashe shi, rumgume ta yayi shima ba shiri ya rad'a mata a kunne "Kin gama dani Hamna, ina sonki kinji." D'ago kai tayi ta kalleshi tace "Muje kayi wanka bawan Allah sai tsami kake." 😂 Bushewa tayi da dariya hakan yasa shi matseta sosai suka shiga d'aki, sosai ta bashi kulawa a wannan lokacin, wanka soso da sabulu haka ta mishi, haka ta b'ata lokaci wajen wanke mishi gasumbarshi da gashin kanshi, hatta aske mafi sirrin wurin dake tara gashi ita ta cire mishi, tun a ban d'aki ta cire mishi akaihu kafin suka fito, da k'yar ya hak'ura ta shafa mishi mai ta caje mishi gashi ta shafa mishi mayukanshi, tana kawo mishi tea mai kauri da zafi ya shanye yaji k'arfi sai fa aiki ya tashi. Ya nuna mata yayi kewarta na sati biyu, ya nuna mata yana son ta kuma yana son kasancewa da ita, ita ma bata tsaya a baya ba ta nuna mishi tayi kewarshi, suna d'aki hankali kwance suna raya zuk'atansu har azahar tayi. Lokacin da zai fita salla ne yake fad'a mata ta shirya yau zasu bar gidan nan tare da yaransu. Ba tayi musu ba dan tasan yanzu su fara tijara da to kawai ta bishi ta shiga had'a iya abinda zata had'a, sauran kuma tace daga baya sun gama d'auka. Baya fitarsu kuma colonel ne ya kira Gambo yake tambayarshi yaya? A cewarshi "Mun dawo, gamu ma gida yanzu." "Ina Hassan yake?" Cewar colonel, ko da Gambo yaji haka yasan babu arzik'i, mik'awa lieutenant wayar yayi yace "Gashi kuyi magana." Ko da lieutenant ya amsa colonel yace "Hassan ka kyauta, an gode Allah ya saka da alkairi, yau Allah ya rufa maka asiri bana garin nan, da sai na maka k'ullin tsiya a ciki har ka amayo hanjin ka." Cikin fad'a lieutenant yace "To bismillah, dan kaga bamu kusa shine zaka fad'a min magana, to ka zo kayi abinda za kayi." Shima cikin fad'a yace "Yo mu ba abun kunyarmu bane wai d'an mu a rufe, kasan irin kunyata mun da kayi?" "An je an kunyata kun, d'an iska ne ni to da zan tsaya ina lallab'a shi, Labaran fa shaidata ne nan muka je yaron nan ya bayar da hak'uri a gama komai amma ya k'i, to ya zamu mishi?" A hassale yace "Hak'uri? Ya bawa uban wa hak'uri? Lusari ne shi da zai bayar da hak'uri? To ni daya bayar da hak'urin ma da sai na d'aga mishi nono." 😂 Da sauri lieutenant yace "Sakarai ina kaga nonon to? Kenan ka d'aure mishi gindi ya ci gaba da d'aukar rigima." "Yo sai me? Mu ba rigimar ce ta kawo mu duniya ba? Kaga malam karka k'ara mana irin haka, a irin wannan lamarin ba'a ma yaro haka, yanda yake da laifi shima waccen yaron da laifinshi, tunda waya aike shi kula masa matarshi sannan yasa aka ma d'an uwanshi duka, da kaima ka tsaya a wajen ka kare d'anka ka nuna musu ba bare bane shi ko marar gata, amma saboda Allah saika wulak'antashi a gaban mutane." Cikin jin haushi yace "To ubana, yanzu yanda za ayi idan zaka dawo ka taho da bulala sai ka zaneni." "Yo kaine da girmanka zan tsaya sawa bulala? Me ye anfanin bindiga ta to? Ai saidai kaji alburushi tsakiyar zuciyarka." Zaiyi magana Gambo da yaga abun ya k'i k'arewa ya figi wayarshi ya d'ora a kunne yace "Malam idan fad'an zaka masa ka kira shi da wayarka amma ba da kud'i na ba." "Au Gambo ni zaka ma iskanci? To kud'in ne bana da ko wayar? Kayi sa'a bana gabanka da na fasa wayar, ba d..." Bai barshi ya fad'a ba ya kashe wayar yana dariya. Dan yasan yana can yanzu yana mita da jaraba. *Da yamma* fa tsaf ya shiga ya fad'a musu gidan nan zasu bari, Ummy ce ta kalleshi tace "... *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _77_ "Ammar da gaske kake tafiya zakayi? Amma kai tsaye haka?" Cikin ladabi yace "To Ummy ni kuwa me zan zauna nayi? Ina d'aure fa a gidan nan kuke cin kaji kuna shan faro da exotic, to dan Allah me zan zauna na muku." Hannunshi ta kama ta jashi zuwa d'akinta, saida ta zaunar dashi kan kujera sannan ta sake shi ta samu wuri ta zauna, kallonshi tayi sosai tace "Ammar ina fata dai rigimar nan ta kwanta ko?" Da sauri ya kalleta yace "Ta kwanta Ummy? Haba haba haba, wannan magana ai bata taso ba, kamar fa a dake ka ne kuma a hanaka kuka, Ummy ko mutum na kashe a garin nan wallahi na fi k'arfin wulak'ancin da aka min, dan haka da yaron, da jami'an, da dokar, da wanda ya bayar da shawara aka k'irk'iri dokar, da wanda yayi rubutun dokar, da wanda yana nan aka aza dokar kai har da wanda ya aza dokar ma duk sai..." Da sauri Ummy ta rufe mishi baki tana fad'in "Rufa mana asiri karka k'arasa fad'a, iyayenka ma zasu iya shiga ciki." Jinjina kai yayi irin haba d'in nan, d'auke hannunta tayi ta mishi kallon fahimta tace "Ammar ka yarda ni mahaifiyarka ce?" Jinjina kai yayi yace "Na yarda mana Ummy." Kai tsaye ta d'ora da "Kuma ka yarda ina da girma da matsayin da zan iya sa ka ko hana ka?" "Tabbas Ummy, kin isa har ma kin wuce." Jinjina kai tayi alamar gamsuwa tace "In dai hakane to ina so maganar nan ta wuce, wucewa ta har abada Ammar, ka bawa al'amarin nan baya ka fuskanci rayuwarka ta gaba, 'ya'yanka da matarka ka rumgumesu ka watsar da duk wani shirme, idan har ka yarda zaka daina to ina so ka min alk'awarin da zai sani gamsuwa." Da sauri ya rik'o hannunta yace "Wallahi Ummy na miki alk'awari har abada babu ni babu sake fad'a da wani ko tashin hankali, hasalima Ummy ko zagi ba zaki sake ji daga bakina ba, insha Allahu Ummy na miki wannan alk'awarin." Da tsantsar farin ciki tace "Nagode sosai d'an albarka, Allah ya saka da alkairi, Allah ya maka albarka ya kareka daga sharrin masharranta." Shima da jin dad'in addua'r ya amsa da "Ameen Ummy, ni ma nagode." Mik'ewa tayi tana rik'e da hannunshi tace "Tashi kuje Allah ya tsare, Allah kad'e fitina a tsakaninku." Haka suka fito suka tattara yaransu suka fita, ana yan koke koke da yan shak'e shak'e haka dai suka bar gidan da yammar nan kamar wanda aka kora. Yanda Hamna taji ana fad'in gidan ga wanda suka je saida taje ta ga ba haka bane suna k'wauran fassarashi, ba k'arya fa Ammar yayi gini na kece raini na shiga tsara, babu ce kawai babu a cikin gidan amma hatta kayan d'aki saida ya mata sabi ya zuba, har kayan jiki kallonta kawai yake sanda take kwaso kayan jikinsu, bai hanata bane saboda tunanin tana buk'atarsu ne, amma shi babu abinda baiyi ba har yaran ma ya musu sabin kaya. Savon gida sabuwar rayuwar ga sabon k'aramin ciki da take dashi had'e da sabbin mutane, nan suka fara rayuwarsu ta d'aukar bakin duniya da sababi, babu abinda ya rage na zamansu sai ma sababin salon shiririta da suka fito dasu. Idan yaran na gidan kad'ai suke d'an d'aga k'afa suna rage wani abu, amma idan suka fita sai su koma yara sai abinda suka ga dama sukeyi babu mai k'wabarsu. *Wata shida* Yau ma ya gama shiryawa zai fita yara sun kwana wajen Ummy saboda weekend ne, tana zaune ta d'ora farantin kankana kan tulelen cikinta tana sha, ko kulata baiyi ba ya d'auki hanyar fita, baki bud'e ta kalleshi da mamakin yanda ya shareta zai fita tace "Toh! Su Ammar kuma ko magana babu shine zaka fita?" Ba tare daya juyowa ba yace "Bani da lokacinki ne." Ido ta zaro ta shiga kiciyar tashi tsaye rik'e da farantin tana fad'in "Wace yar iskar ce?" Juyowa yayi ya kalleta, a hankali ya shiga takowa da wani irin kallo mai d'auke da salon mugunta, da sauri ta shiga ja baya ta fara zagaya kujerar tana fad'in "Allah karka matso nan Ammar, ka tsaya nan ka fad'a min wace shegiyar ce ta d'auki hankalinka har tasa kake jin baka da lokaci na." Cikin dakiya yace "Zan zo ne nan saina fad'a miki yanda zaki fahimta." Da sauri tace "Daga nan ma idan ka fad'a zan ji, fad'a min wacece ita?" Da sauri ya d'ago k'afa da niyyar kamota hakan yasa ta juyawa zata zuba a guje d'aki, cikin d'aga murya yace "Hamna in kika tafi a guje da cikina ban yafe miki ba." Da k'arfi ta juyo tana kallonshi tana ja baya da tsoron kar ya tardata, da k'arfi ya rik'o wuyan hannunta yana matsewa cikin k'eta yana fad'in "Ni na fad'a miki ina da yar iska ne a waje? Wai ke me yasa kishi ya miki yawa ne?" Cikin zabga ihu kai kace idonta yake cirewa ta shiga fad'in "Ammar zaka karya min hannu, sake ni dan Allah sake ni, hannu na fa zai karye." Saida ya zaunar da ita kan kujera yayi tsaye k'ik'am a kanta, ko da taga ya fara saita yatsunta tasan me zaiyi, zillewa ta fara yi tana kokawar k'watar hannunta tana fad'in "Na daina na daina, yi hak'uri ba zan sake ba, dan Allah yatsuna fa zasu karye." Ai kuwa bai kulata ba ya shiga lank'wasa yatsunta yana tausasu suna k'ara da k'arfin tsiya ba tare da sun shirya ba ji kake k'was k'was k'wask'was, saida ya gama ya saketa ya sunkuya ya kama na k'afa, billi ta shiga yi da k'afafunta tana fad'in "Na tuba Ammar na tuna na tuba wallahi." Saida ya gama tas ya mik'e ya gyara zaman rigarshi ya sunkuya ya sumbaci kumcinta yace "Je t'aime." Juyawa yayi zai fita ita ma ta mik'e ta nufi d'aki, saida ta kai k'ofar d'akin shima ya kai k'ofar fitar tace "Duk yarinyar daka kalla ko ka bata hannu kuka gaisa ban yafe maka ba Ammar." Lumshe ido yayi ya juyo kamar mai jin bacci ya kalleta, gwalo ta masa tace "Naje na fad'a ka zo mana." Gyara tsayuwa yayi yace "Ni kuma yau in na fita sai nayi budurwa, kinsan dai ba zan zauna dake kad'ai ba haka kawai, kamar yanda nake canja abinci na haka ma ina buk'atar canja wurin hutuna, dan haka zan samo yar yarinya yar cakwai da zan iya d'auka ba tare da nayi nishi ba, ke kuma a lokacin zaki san girman da nake da shi." Hamna da taji kamar ya soketa da mashi da sauri ta manta da wajen b'uya ne ta nufa ta fito ta nufe shi gadan gadan tana shiryin kuka tana fad'in "Ammar Ammar, zo dan Allah muyi magana, zo na baka hak'uri." Juyawa yayi cike da jin wata isa da izza wai shima akwai wanda yake wahalarwa akan son shi ya nufi k'ofa, da sauri kamar zatayi gudu ta riskeshi yana shirin shiga gabjejiyar motarshi fara tas, rik'eshi tayi ta baya tana turo baki, juyowa yayi ya kalleta fuska a had'e yace "Ya dai malama? Sake ni sauri nake." Ba tare data saki rigarshi ba taja ta har k'asa ta durk'usa gabanshi ba tare da jin nauyin cikinta ta marairaice tace "Ammar karka min kishiya ko ta waje ce dan Allah, ina sonka ba zan iya rabaka da kowace mace ba wallahi, dan Allah kayi hak'uri ka fad'a min duk abinda kake so da wanda baka so zan yi wallahi." Saida yayi da gaske ya cije dariyar dake son taho mishi, kallonta yayi yana d'an basarwa yace "Kin tabbatar za kiyi komai nace miki?" "Allah kuwa zanyi, na rantse maka." Kamo hannunta yayi ta mik'e yana kallon fuskarta yace "Da fari ina so ki daina kirana Ammar gatsau babu sayawa, in baki manta nasha fad'a mikibana so, amma dana ga kin k'i dainawa saina zuba miki ido." Da tsantsar gaskiyar dake tattare da ita tace "Allah daga yau ba zake sake jin baki na yace hakanen ba, *duniya ta*, nima zanyi kamar yanda yer uwata ke yi." Ajiyar zuciya ya sauke cike da k'aunar wacce ta ambata yace "Allah ya gafarta mata." Kamar za tayi kuka ita ma tace "Ameen." Kallonshi tayi tace "To sai me kuma?" Kallon fuskarta yayi yace "Ko daina min rashin kunya, bana son ina cutar dake." A marairaice tace "Shi ma na daina." Murmushi yayi ya shafi fuskarta yace "To shikenan babu ke babu kishiya ko ta cikin gida ce barz ta waje, yanzu kije ki huta abinki kafin na dawo na tayaki hira." A sangarce tace "Ka kula min da kanka." "Ke ma ki kula min da kanki." Ya fad'a yana shiga motar, ta cikin gilashi ya bita da kallo har ta shige kafin ya tayar mai gadi ya bud'e masa k'ofa ya fita. Dariya kawai yake shi kad'ai Hamna ce durk'ushe a gabanshi, yana sonta kuma ya yarda ita ma tana son shi, yana jin dad'in zamantakewarsu kuma yana alfahari da hakan, sau da dama sukanyi fad'a har ta kai basa kula juna, amma ko awa basa yi suke shirya kansu cikin sauk'i, wani lokacin ma daga inda aka samu sab'anin ake d'inkewa ya shiga wainata yana rawa da ita ko ya goye har su shirya, hakan ne yasa zaman nasu dad'i da fahimtar juna. *Kamar* tsautsayi kam akan hanyarshi sai ga d'aya daga cikin mutanen da har yau idan ya tunasu sai yaji kamar yayi kuka, kaf tsawon rayuwarshi babu wanda suka tab'a wulak'antashi sama dasu, ba'a tab'a mishi cin zarafin da suka mishi ba, ba'a tab'a mishi abinda bai rama ba, amma su sun sha daga kalaman mahaifiyarshi, alk'awarin daya mata ya tseratar dasu daga d'aukar fansar shi. Amma kuma yanzu ga d'aya a cikin jami'an da suka dinga hantararshi da hana shi abincinshi, yana gaba akan mota yana birka gudu sosai da hular kwanon da ba mai rufe kai ba duka, d'an lumshe ido yayi tare da bud'ewa yace "Ummy ki gafarce ni, wallahi zuciyata tsayawa za tayi idan ban d'an tokareshi ba." Yana fad'a ya jawo belt d'inshi ya mak'ala sai kawai ya k'ara gudun motar, saida ya daidaici tayar moton kawai ya zungureshi, sai kawai ji akayi gijim ya wuntsile ya fad'i kan moton, da sauri ya taka birki haka mutane dayawa ma duk aka zagaye shi ganin soja ne fan a cikin tenue yake. Da sauri ya fito daga motar yana réaction irin abun a bazata ne ya zo, ko da ya k'araso wajenshi suka had'a ido sai yace "Yallab'ai, kai ne ashe? Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, na shiga uku yau, sannu yallab'ai dan Allah kayi hak'uri, wallahi..." Bai barshi ya k'arasa ba dan shi kanshi ko da ya ganshi a ranshi ma yace ai dole ya hak'ura, mik'ewa yayi cike da dauriya yana fad'in "Kai haba ba komai Elaji, tsautsayi idan ya wuni baya kwana ai." Hannunshi ya damuk'o ya rik'e sosai yana fad'in "Wallahi hakane, kawai wata waya ce aka min da nake da tabbacin ba lafiya ba, kasan ai ita yar gwamnan naku nake aure, to ita ce na baro gida da tsohon ciki, shiyasa hankali na baya kwanciya idan na fito." Murmushin dole ya mishi yace "Ah to Allah yasa alkairi, Allah ya raba lafiya, ba komai kaje kawai." Da sauri yace "A'a ka bari na aje ka asibiti ko?" Shima da sauri yace "A'a wallahi ka barshi, ai banji ciwo ba." Mik'ewa yayi ya mishi sallama ya juyo zai koma mota, murmushi yayi murya k'asa k'asa yace "Da ubanka ne zai kaika asibitin, daka yarda ka shigo mota ta da nufin na kaika asibiti da sai dai a wuce da kai morgue daga nan, kad'an ma ka gani wallahi Ummy ta cece ku." Bayan ya dawo daga inda yaje gida ya wuce, yara na ganinshi suka ce ai sai dai ya koma dasu, da k'yar ya lallab'asu suka rabu, saida ya keb'e da Ummy yace "Ummy dan Allah ki yafe min duk laifin da kika san na miki, kina sane ko rashin sani." Da murmushi a fuskarta tace "Ba komai Ammar, na. yafe maka duniya da lahira." "Nagode Ummy." Ya fad'a yana musu sallama ya bar gidan, saida yaje ya samu Hamna ya shiga fad'a mata abinda ya faru dalla dalla sala sala, ita dai tayi dariya kamar cikinta zai fashe, daga bisani kuma ta raka shi addu'a. *Rayuwa kenan*, abun kamar jiya ne aka fara sai gashi yanzu da aurensu *shekara uku* kenan, yanzun ma namiji ta haifa wanda ya ci sunan *Hassan* suke mishi alkunya da *Elhaj*, Ammar ya tayar da billi shi fa yan uku yake so ya haifa, Hamna kuma dake k'ok'arin cika alk'awarinta duk in yana tijara yanzu sai dai tayi gum da baki tana saurarenshi, in yayi ya gaji sai ya koma ya fara juye mata yana kiran ta raina shi ta d'aukeshi mahaukaci ne, duk da haka bata kula shi sai dai ta bar mishi wajen har sai ya gaji dan kanshi. *Yau* hankalin Jibril in yayi dubu ya tashi, yarinyar da yake saka mata ido, yarinyar da duk inda zata je tare da dreba take, amma aka wayi gari da sunan taje école kawai ya had'e da ita a wani babban store tare da k'awayenta da kayan makarantarsu alamar daga can suka wuce, hakan na nufin tana fita daga makarantar kenan? Ya so mata dukan mutuwa sannan yaji daga ina suke kuma ina zasu je, amma Jamila ta shiga tsakani tace ba za ayi haka da ita ba, tunda tace abu suka je siya kuma su koma kawai ya hak'ura, amma tsoron kar wani ya mishi kutse a rayuwar yarinyarshi da kuma kiyaye maimaituwar tarihi sai kawai ya yanke wani tsatsauran hukunci a kanta. *Sadiq* zaman d'a yake ga Husseina, ya yarda da yaron yana d'aya daga cikin masu kula mishi da mangazarshi da ake aje kaya, ganin tunda yan uwa ne kawai yasa shi cewa in yana sonta ya bashi aurenta, yaro ya ga banza ta ina zai bijire? Sai kawai yace yana so shima ya amince, kamar wasa sai manya suka shiga maganar akayi komai a gaggauce, inda yace zata kammala karatunta a gidan mijinta. *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _78_ *Zo* ka ga uban amarya uban d'aurin aure Ammar, shi Jibril ya bawa d'aurin auren wanda hakan ya masa dad'i, Mari tayi jarabar a kai mata Huda ayi biki ranar bikin sai a dawo da ita, amma Jibril sam ya gama fita harkar Mari yace ai kawai ta zo in tana so amma babu inda Huda zata je, har Amar saida ta ma magana a waya wai ya lallab'ashi, amma shima hak'uri ya bata yace Jibril bai amince ba. *Yau* d'aurin auren Huda, Ammar ya kashe d'aurin hula ya k'ayatu cikin babban riga ta wani gallelen boyel bleue bics, ya gama had'uwa da tsaruwa fiye da ma angon. Hamna ma ta gama shiryawa cikin shaddarta gezna colour bleue omo zasu tafi tare, tsaye suke dukansu gaban madubi yana ci gaba da gyara zaman hularsa, ita ma kallabi ta gama d'auri ta d'auki turare zata fesa ya fige yace "Turaren me kike buk'ata?" Kallonshi tayi tace "Cikin mutane fa zan shiga." Shareta kawai yayi ya aje kwalbar ya d'auki na shi turaren zai fesa, da sauri ita ma ta fige tana ja baya da gudu tana fad'in "Tunda ban saka ba wallahi kai ma ba zaka saka ba, duk mu tafi haka." Juyawa yayi ya kalleta yace "Hamna kawo min turaren nan." Hanyar fita tayi tana fad'in "Ba zan bayar ba Allah." Ko da ta fita d'akinshi ta nufa da niyyar shiga ta rufe ta d'auke turarukan dake nan, dan tasan su zai nema duk da dai yafi aikida wanda ke d'akinta, amma kafin ta rufe ya biyota yana tattare babbar rigar yana fad'in "Ke in rashin mutumcin kike ji saina kwab'e wallahi mu daku yanzu nan." Baya tayi tana fad'in "Me yayi zafi da zamu daku ni da kai? Turare dai ne ba zaka saka ba kai ma in dai ban saka ba." Ko da taga ya tafi a guje zai kamota saita tsorata kawai ta buga kwalbar k'asa ta kuwa fashe saboda akan tiles ne babu carpet wurin, bud'e baki yayi da ido yana kallon kwalbar. Saida ya b'ata rai ya kalleta yace "Hamna ni kika fasawa turare? Ni Hamna, ai ko zaki ga rashin mutumci a gidan nan." K'uri ta masa da ido tana so tace ba dagangan tayi ba amma ta kasa, cire babbar rigar yayi ya aje kan gado ya tunkareta, ihu kawai ta saki dan ba zata iya guduwa ba kan hanyar fitar yake tsaye, saida ya tak'ark'are yasa k'arfi ya kimkimeta gaba d'aya, bai tsaya komai ba ya shiga wani irin juyin bala'i da ita yana hajijiya, tun tana ganin d'akin tana gane komai, har saida jiri ya d'ebeta ta dinga ganin d'akin na juyawa gaba d'aya. A hankali taji kamar kanta zai cire duk tunani da lissafinta sun fara barin kwanyar kanta, rik'eshi tayi gam ta rintse ido tana jiran ranar da zai sauke ta, saida ya gamsu cewa ta kuru yanzu kad'ai ya direta k'asa, ganin wani luuuuu da tayi kamar zata kifa yasa shi b'anb'are hannayenta data rik'eshi gam, ai tuni d'aurin d'an kwalin ya rigata kaiwa k'asa duk suka watse a wurin, dafe k'asa tayi sosai saboda har yanzu juyawa ake da ita. Rigarshi ya saka ya kalleta yace "Idan ki kayi wasa Hamna d'aurin auren nan da za ayi har da nawa za'a d'aura, kuma ke nake jira karki b'ata min lokaci." Saida ya kai k'ofa zai fita ya juyo yace "Amma Hamna Allah ya saka min wannan wulak'ancin da kika min, yanzu waccen turaren kike sona saka mai warin yan wuta?" Hamna da a lokacin kad'ai ta fara jin dama dama kallonshi tayi tace "Kenan kasan k'amshin yan wutan?" Saida ya wani had'e fuska yace "Ina d'an ji kad'an kad'an." Mik'ewa tayi tana ganin yana juya mata a hankali tace "A jikinka kake ji ko?" 😂😂😂 Da sauri ya dawo d'akin yana fad'in "Fito kai tsaye kice d'an wuta ne ni mana." Hannayenta ta d'aga tana tare shi dan ba zata iya gudun ba tana fad'in "Ni fa tambayarka ne nayi a jikinka kake ji ko a jikin wani." Juyawa yayi zai fita yana fad'in "Kinyi sa'a yau nake aurar da 'ya wallahi, da sai na miki cikin yan uku." K'eyarshi ta ma gwalo tana fad'in "To inba d'an wutar ba wannan jirin daka d'iba dani kamar wacce ta hau jirgin sama." Tafiya suke a hanya tana d'aura d'an kwali, cike da nishad'i yake biyar wak'ar wani film wai ita *madubin dubawa* wacce Ali Nuhu da Rahama Hassan sukayi play roll d'in, yana biya kamar abun gaske, amma daga jin baitin da jarumar ta fad'a ya kalli Hamna yace "Kinji wai ta sauke farashi, yo shi ba dan ma ana so a bada maza ba wane farashi ne har mace zata kallemu tace ta sauke, ke baki ga inda muke tsada ba ma ku ne ke biyanmu sadakin." Shiru ta masa tana d'aura kallabinta kafin ya sake cewa "Kuma fa ita ba wata kyakyawa ba banda dai Allah ya taimake ta tana da manyan kaya." Kallonshi tayi ta harareshi sama da k'asa tayi k'wafa, kallonta yayi yace "Me ye na hararata ke kuma?" Saida ta gyara d'an kwalin tace "Inba gulma ba da sa ido har ka mata kallon k'waf ka gane manyan kaya ne da ita ko?" "To makaho ne ni?" Ya fad'a yana kallonta, a hassale ta kalleshi tace "Ba mahako bane, amma idan na cire maka su zaka dawo makahon." Wani kallo ya mata yace "Wai ke mayya ce?" "Eh." Ta fad'a tana kumbura, tab'e baki yayi yace "Wai ma me ye farashin da take magana akai?" Kallonshi tayi tace "Ka tambaye ta mana." Tab'e baki yayi yace "Wai haushi kike ji saboda naga ita ma k'atuwa ce kamar ke? To naje na ce a dafani a cinye." Wani kallo ta masa bata sake cewa komai ba har suka isa. Yau fa akayi ta kam a wajen d'aurin aure, bayan an d'aura ya shigo da ango har cikin gidan, har d'akin Ummy inda amarya take ya zaunar dasu, hud'uba ya musu sosai mai ratsa jiki, saida ya gama kamar abun arzik'i sai kuma ya kalli Huda yace "Kina ji na? Duk sanda ya guma miki laifi ki zo ki same ni, sai kin fad'i yanda kike so na miki dashi, in na dafa miki shi da fatar jikinshi ne, ko kuma sai an cire fatar a dafa sai kin zab'a." Ango dai murmushi ya saki inda ya kalleshi shima yace "Kai ma kuma idan ta b'ata maka, ka zo ka same ni zan fad'a maka yanda zakayi da ita." Kud'in hannunshi ya mik'a ma Huda yace "Karb'i nan sadakin ki ne." Cikin lullub'inta na dara tace "Abba ka rik'e kawai, ni babu abinda zanyi dashi." Kallonsu Ummy dasu Zeinabu yayi yana dariya yace "Kunji wai Abba, yanzu nan fa ya ce na aurar, kai Allah nagode maka, yanzu nan da yan shekaru kad'an Amnata ma zan aurar da ita." Kallon Huda yayi ya kamo hannunta ya damk'a mata kud'in yana fad'in "Wannan sadakinki ne, kamar yanda mijinki ne kad'ai ke da wani muhimmin hurumi akan ki yanzun, haka wannan kud'in ma ke ya dace ki rik'e abinki, lada ce ta wani muhimmin abu da zaki rasa a jikinki." Sautin kukanta ta k'ara hakan yasa shi dafa kanta yana fad'in "Kar kiyi kuka mana, ni ma saiki saka ni kuka." _(Allah ya bar mana kai kakanmu Tahir, ka iya wakilci)_ Saida ya kai k'ofa zai fita ya kalli Zeituna yace "Uwa wai me yasa amare ke kuka ne? Wani abu suke tsoro ko kuma fargaba ne?" Da kunya ta shiga rarraba ido ta kalli Ummy tace "Aunty ce zata fad'a maka." Da sauri ta bar wajen Ummy na fad'in "Ke dawo ke zaki iya da kayanki, ai ba ni ya tambaya ba." Murmushi ya saki yana kallonta yace "Ummy na ma gane, to amma naga ai daga baya kuma idan kuka saba kun ma fimu zak'ewa." Da k'arfi ta dafe k'irji tace "Mu kuma?" Cikin i'ina yace "A'a ina nufin su, su matan." Ficewa yayi ta bishi da kallo, ko data hange shi tsaye kan Hamna dake shirya yaransu da suka kwana anan tace "Allah fidda *A'i* daga rogo." *Badak'ala na ban kwana insha Allah* *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ _79_ Ana ta cashewa a wajen bikin Hamna na zaune k'ofar gida tare da wata k'anwar Soueiba, ta baza mata hajar kayan mata tana dubawa inda Ameera ke kusanta tsaye, Ummy ce zata shiga cikin gidan ta kalli Ameera tace "Wai ke yaushe zaki girma ne? Kina nan k'ugunta ba zaki je cikin yara kuyi wasa ba." D'agowa Hamna tayi ta k'ara mannata a jikinta tana fad'in "Ummy ki barta dan Allah, ni kaina bana so tana min nisa ai, mace ce dole ina buk'atar tafi sabawa dani fiye da kowa." Tab'e baki Ummy tayi tace "Amma kuma bata sakewa cikin yara taya za tayi wayo da fasaha?" Turo baki Hamna tayi tana kallon Ummy har ta wuce, kallon Ameera tayi ta manna mata sumba a kumatu tana fad'in "Ai kina da wayo ko?" Kallonta tayi tana mak'ala hannayenta a wuyan Hamna tana dariya da fad'in "Ummy, in fad'a miki wani abu?" Kallonta tayi tace "Fad'a min mana yer uwata." Saida ta kalli k'anwar Soueiba dake ta mik'owa Hamna magani tana karb'a tana dubawa, cikin kunne ta rad'a mata magana, bud'e baki tayi da dariya a fuskarta ta kalleta tace "Da gaske? Haka yace miki?" Cikin jin kunya ta rufe fuskarta da kallabin Hamna, jinjina kai tayi tana fad'in "Ina ga fa za ayi yar gida ce ko?" Dariya suka saka gaba d'aya, tana cikin dubawa ta ga motar Ammar ta paka, da sauri ta shiga tattara kayan tana fad'in "Taimaka b'oye kayan nan kar mutumin nan ya sauke min kwadon tsiya a wurin nan." A tsorace matar ta shiha tattarewa tana fad'in "Baya so kina aiki dasu?" Saida ta gyara zamanta tana kallon motar tace "Ba haka bane, bana so ya sani ne kawai zai min tsiya wallahi." Suna kallo ya fito ya canza kaya bana safe bane jikinshi, a hankali Ameera ta tarbeshi inda ya kamo hannunta suka k'araso, yana zuwa ya dangwari kan Hamna yana fad'in "Kankana me kike fad'a ma 'yarki naga kuna ta dariya?" Matar na kallonshi tana musu dariya sai Hamna data dafe kanta tace "Yaushe?" Kallonta yayi yace "Ke ni ba makaho bane ina gani, me kike fad'a mata?" Turo baki tayi tace "To wai banda ikon da zanyi magana da "yata ne? Sirri mukeyi mana kai ma kaje ka kama naka yaran mana." Tab'e baki yayi yace "Ke dai kika sani, yanzu tashi shiga cikin gida." Da sauri ta mik'e tana fad'in "To yallab'ai." Kallon mai maganin tayi ta k'yabta mata ido ta shiga ciki tare da Ameera, a baya ya bisu yana fad'in "Yau ma ana bikin ba zaku rabu ba? Wai ke wace jaraba ce kika koyawa yarinyar?" Gum tayi da baki dan ta fahimci me yake nufi, tayi magana ne ya fara tayar mata da hankali cikin mutane, rik'o mayafinta yayi hakan yasa ta juyowa tana kallonshi, kallonta yayi yace "Yunwa nake ji." Wani kallo ta masa tace "To ya zan maka kenan?" Shima wani kallon ya mata yace "Ya rage naki." Wucewa yayi tana kallo har yayi bayan gidan, tasan kuwa d'akin lieutenant zai je ya zauna jiranta, girgiza kai tayi suka wuce ciki, inda ake girki taje ta samu an idar amma ana so ayi sallah la'asar sai a raba, plate ta samu ta zuba masa taje ta kai masa, har zata fita daga d'akin yace "Ke." Saida tayi jim saboda ta tsani ya kirata da ke, juyowa tayi tana kallonshi yace "Zauna ki bani a baki." A marairaice ta kalleshi tace "Yallab'ai biki fa ake gidan nan, kar kasa a saka mana ido mana, dan Allah ka ci abincin kai ma ka fita kafin ayi sallah." Wani kallo ya mata yace "Yanzu Hamna saboda bikin ne yasa ba zaki bani abinci a baki ba? Bikin ya fini mahimmanci kenan?" Tahowa tayi a k'ufule ta zauna ta jawo plate d'in zata bashi, mik'ewa yayi yana kallonta yace "Ke ni ba d'an iska bane, kawai daga bani abinci a baki shikenan na miki laifi, to bana ci Hamna." Har ya juya zai fita da sauri ta mik'e da niyyar taroshi ta bashi hak'uri, sai kuma ya juyo a hassale yace "Ki same ni a mota yanzu har ke ba zaki zauna a wajen bikin ba." Juyawa yayi ya fita hakan yasa ta dukan cinyarta cikin jin haushi, kai da kawo ta fara a d'akin tana tunanin abinyi, da sauri ta zabura ta tafi da sauri zuwa fita kafin tayi wani laifin, haka ta ratsa mutane ta fita ta same shi. Tunda ta shiga motar babu wanda ya kula wani har suka kai gida, ta riga shi fita ta nufi hanyar shiga cikin jiki a sanyaye, taji sanda ya rufe motar amma bata juyowa ba, sai ji kawai tayi ya fizgeta zuwa cikin gidan da sauri kamar zata kifa k'asa, saida ya tsaya zai bud'e k'ofar da makullanshi ta samu ta durk'usa kan gwiwoyinta ta rik'e k'afarshi tana fad'in "Dan Allah yah Ammar kayi hak'uri, ni wallahi raina bai b'ace ba." Uwar d'aki ya shiga da ita ya shiga bata horo kan abinda ta masa, horon bala'i wanda ta wani fannin gwara duka dashi, ya gama gigitata tare da galabaitar da ita, zuwa ne na k'eta da bak'in ciki yake mata, saida ya gaji dan gaban kanshi kuma ya koma kimtsata da rarrashi wai tayi shiru ta yafe masa. Haka Ummy tayi ta kiranta tana ina sai shi ya fad'a mata ai tana gida, a hassale Ummy tace "Uban me take gidan to bayan nan ana nemanta?" Cikin rarrashi yace "Kiyi hak'uri Ummy zata dawo anjima." Cikin fad'a tace "To me taje yi a gidan ne wai?" Cikin nutsuwa yace "Ummy ibada ta zo, kuma ni da kaina na kawota." Kashe wayar tayi ba tare data k'ara jan zancen ba, kallon Hamna yayi dake kusanshi ta zuba masa ido yace "Lafiyar kallona?" Da sauri tayi k'asa da idonta, k'ura mata ido yayi shima yace "Kina lafiya?" Ba tare data kalleshi ba tace "Bana jin dad'i k'asa, ka mayar dani gida ina so na ga Ummy." Kamar daga sama kawai taji ya bud'e mata k'afafu ya zura hannu yana fad'in "Bari na duba ki watak'ila k'ari kikayi." Rintse ido tayi tana jin zafi duk inda ya tab'a, saida taji ya ciro hannunshi ta bud'a ido, gani tayi ya kafeta da ido yana kallo, jawo kanta yayi cikin kunne ya rad'a mata "Kin fiye zak'i da d'and'ano ne, uwa uba ga ruwa." Kamar yau ne haka ta fara faruwa kawai sai taji kunya ma ta rufe ta, sunkuyar da kai tayi hakan yasa ya sumbaci goshinta yana fad'in "Kankana ta uwar ruwa, a ci gaba da shan kankana ba d'aga k'afa, ni ma ba zan gaji da kawota ba, haka kuma ba zan gaji da tsotsar ruwana ba." Mik'ewa yayi ya shiga d'akin daya ware na magunguna, ba jimawa ya fito sai ji tayi ya kwantar da ita yana gyara zare da allura, da sauri ta tashi tana fad'in "Me za kayi kuma?" Hararanta ya shiga yi sama da k'asa yana fad'in "D'inki zan miki, kin k'aru Hajiata." Girgiza kai ta shiga yi tana fad'in "A'a wallahi bana so, ni ka bari Ummy na zata min, bana so gaskiya." Sake kwantar da ita yayi yana fad'in "Ni kuma ga mahaukaci kullum sai mu tsaya Ummy ce zata dinga d'inke b'arnar da d'anta ya aikata ko? Ai ko ban iya d'inkin ba kinsan na koye shi dan na dinga gyara kayana da kaina, bare kuma na iya har tiyatar zuciya na iya." Tana kuka tana k'ari tana ihu tana bata so tana rirrik'e shi haka ya mata d'inki uku, saida aka gama ta yunk'ura da k'yar ta tashi zaune wai sai gani tayi yana share hawaye (D'an iska rairai ne😂), da mamaki tace "Lafiya kake kuka kai kuma?" Kawai fad'awa yayi kan k'afafunta har da jan majina yana fad'in "Wallahi tausaya miki nake, akwai zafi d'inkin nan, sai naji kamar a zuciyata nake soka allurar da zaren." D'ago kanshi tayi tace "A kaina ne dama kake kukan?" Turo baki yayi yace "Ina sonki sosai Hamna, duk abinda zan miki da zai cutar dake ba nayi shi dagangan bane, b'acin rai ne ke saka ni, ki yafe min kinji." Jawo kanshi tayi ta manna a tsakiyar mamanta tana shafa kanshi tana fad'in "Kayi hak'uri ai nice mai laifi ni ce bana jin maganarka, kuma duk horon da kake min ina jin dad'i dan hakan yana nuna min ka isa dani ne, sannan ina d'aukarshi a matsayin horo na yaya da k'anwarsa, dan haka ka daina zubar min da hawayenka na cancanci wannan hukuncin, ko ba komai kaga gobe zan kiyaye fito da b'acin rai a fili yayin da ka saka ni aiki." D'ago ido yayi ya kalleta cike da k'aunarta yace "Yunwa nake ji fa." Hannu tasa a rigarta tana fito da nononta tana fad'in "To dama me ye anfanin nonon da har yanzu yake min zuba? Saboda kai dama nake ta ajiyarshi." *Iko sai Rabba*, k'ato ya daddage a k'afafun yarinyar sai tsotsar nono yake, rayuwa kenan ta musu dad'i, komawar da bata yi ba kenan wajen bikin nan sai dare, a lokacin da suka je har an zo d'aukar amarya, ko da ya sauketa yace "Ki kula min da kanki Hamna." Kallonshi tayi tace "Kaima ka kula da kanka, amma ana zaka jirani har mu dawo sai mu koma gida ko?" Saida ya kalli gabanshi yace "A'a, daga nan majalisa zan tafi, akwai wad'anda na gayyata d'aurin aure kuma ban gansu ba, to zan je ne na shukawa kowa rashin mutumci, sannan su biyani katin d'aurin aurena dana basu, tunda 'ya'yan k'ananan mutane ne su." Kafin tayi magana ya ja mota ya wuce, da kallo ta bi motar tana mamakin abinda zaije yayi, bata ankara taji an daketa a baya da sauri ta juyo ta ga Sayyada, hararanta tayi tana fad'in "To dad'i miji sai yanzu kika dawo?" Murmushi ta mata tace "Kin fad'i daidai, mijina miji ne da zan iya kiranshi namiji gaban zaratan maza." Dariya tayi tace "Ba sai kin fad'a ba ai, kowa ya ganshi zai gane hakan, shi yasa ma nake nan har yanzu banyi aure ba shi nake jira yayi ta biyu dani." Wata harara ta galla mata tace "Sayyada rufawa kanki asiri wallahi, mijin nawa? Ai kuwa sai dai ki mutu babu aure." Dariya tayi tace "Au ba'a aure ke ya aure ki?" Kallonta tayi sosai tace "K'addararsa ce ni babu yanda zaiyi, ke baki ga yer uwata ba ma aka raba shi da ita saboda ni." Yanda Sayyada taga duk tayi ne yasa ta daddab'a kafad'arta tana fad'in "Sai hak'uri Hamna, ki ci gaba da mata addu'a." Saida ta goge k'walla tace "Allah ya jik'anta da rahama." "Ameen ya Allah." Ta fad'a kafin ta d'ora da "Haka naji mutane na fad'a, ashe kema kin fahimci haka." A nutse ta kalleta tace "Sayyada kullum na kalli Ameera sai na ga fuskar yar uwata a fuskarta, kuma kullum na ga haka saina tuna rayuwata da ita, haka zalika ina tuna cewa tsananin rabon haihuwar dake tsakani na da yah Ammar ne ya amshi rayuwarta." Jinjina kai tayi tace "Hakane, kinsan shi rabo ba'a rantsewa akan shi, da wani yayi k'ok'arin shiga tsakaninku to sai dai ya mutu." Kama hannunta tayi tana fad'in "Muje ciki na samu zagina a wurin Ummy tun yanzu, yau nasan har uwata sai Ummy ta ci." Cike da raha tace "Ai ko ni zan kama mata, kina matar uban d'aurin aure ace anyi biki babu ke." Bushewa sukayi da dariya inda Hamna tace "Kinsan kuwa mutumin naki ya tafi majalisarsu wai zaiwa duk wanda bai zo d'aurin auren ba rashin mutunci, sannan su biyashi katin d'aurin auren daya raba musu." Girgiza tayi tana dariya tace "Yer uwa wannan mijin naki ki dinga tofa masa lahaula kowace safiya, sannan ki dinga binshi da ayatul kursiyu dan bai rasa shafar mutanen b'oye." Hararanta tayi tace "Sayyada bana son iskanci fa, mijin nawa?" Cikin dariya tace "Ai ni labarinku ma zaki ban wallahi ina da marubuciyar da zata rubuta min shi." Dafe k'irji tayi tace "Ni? Rufa min asiri, idan ya gani babbaka ni zaiyi da raina." "Ba wani nan, ni zanje har gidan na same shi sai ya yarda ko baya so." Dariya tayi tace "Gaki gashi ne ai kar tasan kar." *Ammar* na zuwa duk ya tashi hankalin bayin Allah, kububuwa ya dinga musu ai duk sai ya ci ubansu tunda basu je d'aurin auren fari daya fara ba, sannan su tattara mishi katinshi su bashi inba haka ba zasu ga tsiya, su uku ne a wurin da basu je ba su dai hak'uri suke bashi amma da yake sauran da suka je suna zuga shi saiya dinga botsarewa, fad'i yake ai basu da mutumci ne shiyasa suka mishi haka, kenan ko auren Amreerarsa ya tashi haka zasu mishi? K'arshe dai yace a bashi katinshi kad'ai zai hak'ura, biyu daga ciki har motarsu suka duba basu ga katin ba suka ce bari suje gida su d'auko. Rigarsu ya rik'e yace "Yo ni saida naje gida na d'auko muku? Anan na baku nima anan zaku ban kayana." D'aya ne yace "To ai shine zamu d'auko maka a gidan ko." "Ban yarda ba, a bani yanzu kawai hankali ya kwanta, ko a biyani da kud'i." Wani daga zaune dake ta musu dariya ne yace "Eh su biyaka da kud'i, kati fa yanzu tsada yake, kuma irin wanda kayi ma na manyan mutane ne mai tsadar gaske, ya kai jaka goma fa wannan." Kallonsu yayi yace "To kunji dai da kunnenku, dan haka a fiddo a bani kud'i na yanzu." D'aya da abun ya dame ni ya fiddo jaka gomar ya mik'a mishi yana fad'in "Allah ya rabaka da wannan jaraba Ammar, wallahi ni daga matata ta farko har ta biyu babu wacce ta tab'a titseni irin haka akan abu, yo ni naga jaraba da zafi zafinta." Saida ya soka jaka gomar aljihu yace "Yo suma sakarkaru ne matan basu san yanda zasu amshi kud'i a hannunka bane." Haka dukansu suka biyashi kud'in katinsu kafin ya rabu dasu, mik'ewa yayi yana fad'in "Sai anjimanku to." D'aya daga ciki ne yace "Allah raka taki gona." Saida ya kwaso shoki ya yarfa mishi yace "Na dai ji, sai dai haushi wallahi." Suna kallo ya tayar da mota yayi gaba, wajen wani mai soya doya da kw'wai da kaji ya tsaya, ya mik'a mishi abu amma kuma bai amshi komai ba ya wuce, saida suka ga ya bar wajen inda wani ya tintsire da dariya yace "Ammar jaraba, Ammar bala'i, Hamna na hak'uri da bawan Allahn nan." Cikin wanda suka bashi kud'in ne yace "Ni yanzu kud'in nan daya raba ni dasu daya bar min kayana wallahi dana bawa amarya data nemi kud'in anko." Wani ne yace "Saika bata wasu mana." Babban aminin Ammar ne yace "Kar ma kace zaka mishi Allah ya isa, kud'inku bashi zai cisu ba, in kuma kayi gardama je ka tambayi Buharin kaji." Tashi yayi kuwa da sauri yaje waben mai doyar Buhari, ko da ya ganshi yace "Mutumin yane?" "Lafiya lau, wai Ammar da naga ya tsaya nan me yace maka?" Cikin murmushi yace "Kud'i ne ya bayar yace duk magidancin da ya zo siyan abu a bashi kaza d'aya." Cikin kafe shi da ido yace "Nawa ya baka?" A tak'aice yace "Jaka talatin." Juyowa yayi yana fad'in "Ta tabbata gaskiya ya fad'a, kud'inmu ne yayi sadaka dasu, to Allah ya bashi ladar da mu baki d'aya." *Ameeeeeeeeen*. *Alhamdulillah* 04/11/2020 à 14:40 - Ummulkhairi: 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BADAK'ALA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *Labarin Gaske* *NA* _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _BA SO BANE_ *3* _D'AUKAR FANSA_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI (sai Allah)_ *6* _JIHADI_ *7* _ITACE K'ADDARARMU_ *8* _K'ANGIN RAYUWA_ *9* _MAATA_ *10* _KAWUNA NE_ *11* _KALLON KITSE_ *12* _AURE_ *13* _SANIN MASOYI (baya da k'ura)..._ *14* _BADAK'ALA..._ *SADAUKARWA GA* 👨‍👩‍👧‍👦 _*AHALI NA*_👨‍👩‍👧‍👦 *ALHAMDULILLAH Allah abin godiya, kamar jiya ne na fara BADAK'ALA yau gashi na kawo k'arshenshi cikin hukuncin mai duka, Allah ya gafarta kuraraina da zunubina, Allah yasa muyi tarayya daku a cikin ladar baki d'aya.* 💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝 ☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️ https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Bismillahir rahamanir rahim_ *FIN* _80_ *Laraba* ce yau amma ko da ya fito zai tafi masallaci ya mik'ar da ita tsaye yace "D'auko hijabinki." Kallonshi tayi tace "Hijabina kuma? Ina zamu je?" Fuskar nan a had'e yace "Hijabinki nace ki d'auko, ko gani kike zan siyar dake ne?" Girgiza kai tayi ta juya ta d'auko hijabin ta dawo, hannunta ya kama har sun kai k'ofa taga ba mota zasu shiga ba, gabanta ne ya shiga fad'uwa ta tsaya tace "Yallab'ai lafiya? Dan Allah ka fad'a min me ke faruwa? Ina zamu je yanzu da rana haka?" Ba tare daya kalleta ba yace "Masallaci." Da k'arfi tace "Masallaci? Yin me?" Juyowa yayi ya kalleta yace "Me akeyi acan?" Cikin tsoron kar ya zabga mata mari tace "Sallah." "To ita zamu je muyi, yan uku nake so na haifa, ko jiya saida Hajia ta min gori wai mijinta kad'ai ke da wannan bajintar, ni kuma ina so na kafa mata tarihi." Karantar yanayinshi ta shiga yi, indai bata amince ba zai ci ubanta, in kuma ta amince zata jawa kanta yan kallo, a k'arshe shi da kanshi zai iya mata hukunci yace ai ta shiga cikin maza, a hankali ta d'an girgiza kai a ranta tana fad'in "Ba fa yau na fara saninka ba Ammar, ka daina wahalar dani." Saida ta dafa kafad'arshi cikin rarrashi da taushin murya tace "Duniyata, kayi hak'uri mana kai ka tafi yanzu, nima zanje nayi sallah nayi mana addu'a, insha Allahu ranar juma'a tare zamu tafi masallaci, amma yanzu kaga ni ba nik'ab gareni ba, kuma maganar gaskiya ina maka kishin kaina bana so kowa ya kalleni." Yanda ta k'are maganar da shagwab'a saiya kalleta yana murmushi yace "Ja'ira kuma fa gaskiyarki, amma gaskiya Allah ya taimake ki dan da ace kin bini kuma naga ana kallonki...hummm da uwar mutum ta haifi wani yau." Wani kallon ba ga irinta ba ta mishi kafin tace "Gaskiya kam, shiyasa nake kiyaye duk abinda zai tayar min da kishinka, ai bana so ka k'ara karya 'ya'yan mutane ba." Dariya yayi yana kallonta yace "Yar banza kice dai ba kya son jaruminki ya sake kwana a gidan maza." Dariya tayi tana fad'in "Ina zan so haka kai ma, Allah yanza ka sake tsokano rigima aka kamaka sai na zubar da cikin nan na jikina." Da k'arfi ya juyo yana kallonta yace "Ciki Hamna? Yaushe ki kayi cikin ban sani ba?" Har ta juya da niyyar guduwa ya rik'o hannunta, da k'arfi ya matseta ya d'aga rigarta yana d'an tausa cikinta, ko da ya kai ga mararta ya danna tayi wata yar k'ara mai d'an k'arfi tare da ja baya, sake rik'ota yayi yana kallon idonta yace "Yanzu kankana dan kar na samu yan ukun shine kika samu ciki da wuri?" Cikin kallon kayi hak'uri tace "Allah ba haka bane, nima ina so ka samu." Sakinta yayi yana fad'in "Uhm, zan dage n ci gaba da addu'a idan ma d'aya ne za'a mayar dashi uku insha Allah." Da kallo ta bishi har ya fice, komawa tayi ita ma tana dariya yau wai za'a kaita masallaci. Da yamm lafiya lau ya fita daga gidan, amma bai jima ba sai gashi ya dawo tunda ta hange shi ya fito daga mota yana kumfar baki ta kama jikinta, ko da ya shigo ciki taji yana ta masifa, zaune yayi k'asan carpet sai fad'a yake, kuma ba komai ya jawo masifar ba si ganin Jano da yayi a gari aka, shine ya tambaya yaushe aka fito dashi aka ce masa ai ya kusa shekara biyu da fitowa, shine fa ransa ya b'ace ya dawo gida ya saukewa mi tsotsai, tana gyaran akaifu sai dai ta saci kllonshi da taga zai kalleta tayi saurin d'auke kanta. Yara ne suka shigo da gudu da ball d'insu suna bugawa, da gudu ta taresu a k'ofar d'akin, Shureim ta kama kunnenshi ta murd'e tace "Saurare ni, kaga ubanku nan ya dawo kuma ranshi a b'ace yake, wallahi ku koma can sam kuyi wasarku hankali kwance, in kuma kuna so jikinku yayi tsami to Bismillah." Saida ya d'an lek'a y hangeshi zaune sai k'wafa yake yana cije leb'en k'asa sannan ya kalleta yace "Ummy wai me yasa Abba ya fiya rigima ne? Sai a b'ata masa rai a waje sai ya shigo nan mu ya balbalemu da masifa." Da sauri ta rufe masa baki tace "Shiii, maza ku wuce." Kallon Ahmad tayi da yanzu shim yake tare dasu tace "Ku wuce kaji yarona." Da gudu duk suka nufi komawa sama, Ameera ta kalla tace "Ki wuce d'akinki bana son wasan nan da maza ayita tsalle tsalle." Jinjina kai tayi ta kama hanya zata shiga Ammr ya fito yana fad'in "Ke dai baki san gaskiya ba a rayuwarki, yanzu waccen da kika koresu su ba yara bane?" Kallonshi tayi a hankali tace "Amma ita macece ai." "To sai akayi yaya?" Ya fad'a da alamar tijara kad'an yake jira, girgiza kai tayi tace "Komai, kawai dai ba zan bar yarinyata bane a cikinsu kowane lokaci." Cikin d'aga murya yace "Kinfi so ku zauna kullum kina koya mata kinibibi ko?" Wani kallo ta masa tace "Yan uwa fa shida gareta kuma duk maza, idan ban jata a jikina ba ya kake so na mata to? Zata zauna tana fad'a musu damuwarta ne su?" Juyawa tayi ta kama hannunta suka shige ciki ta tura ta d'akinta. Kallon juna sukayi shi da Shureim da ko da yaga ya fito ya tsaya, ido ciki ido yake kallonshi babu rusunawa, shi ko a abokanshi yana wuya yag wanda suke kallon juna haka bare uwarsu, amma ga babban d'anshi na kallon idonshi kamar yanda shima yake kallon kowa a haka, hararanshi yayi yace "Kai kuma lafiyar kallona?" Me zaiyi sai kawai ya jawo hannunshi suna gaisawa a dole yana dariya yana fad'in "Haba Abba rabu da su dan Allah, wallahi in kana masifa ba kya kyau, yi dariya mana." Kallon yaron yayi sosai, in yana *masifa* baya kyau? Shine d'ansa ke fad'a masa haka? Lallai *Ammar* d'in da Hajia ke addua'r kar a samu gashi za'a samu. K'ok'arin k'watar hannunshi ya shiga yi yana fad'in "Kai d'an uwarka sake ni, tsaranka ne ni." Rik'e hannun yayi gam yana fad'in "Abba ni fa abokinka ne, fad'a min meye damuwar dan Allah." Fizgo hannunshi yayi yana fad'in "Je ka tambayi uwarka mana." Kallonshi yayi yace "Abba wai me yasa ita Ummy sai tace abbanku? Amma kai sai ka dinga cewa uwarmu uwarmu?" Shima kallonshi yayi yace "Bari to zan ma uwar taku kishiya, kaga sain dinga cewa auntynku." Da sauri yayi tsalle ya mak'ale a wuyanshi yana fad'in "A'a wallahi Abba bari wannan magana ma, karna saukewa yarinya kafad'a." Dariya Ammar ya shiga yi dan yasan a bakinshi yaji kalmar sauke kafad'ar nan, lallai iko sai Allah, yana mak'ale a wuyanshi ya shiga falon dashi yana fad'in "Ke zo ki min tsakani da yaron nan naki, kinga dai kin lalata shi nema yake y zama wani iri." Wani kallo ta masa tace "Kai da kan irin hka way rabak da Abba? Dubarun zama dashi kawai zaka koya kaima, dan ba lallai kayi hak'uri kamar yanda su Abba sukayi ba." Zaune yayi dashi suna hira da k'yak'yata dariya, duk abinda Ammar ya fad'a Shureim na da amsa ko abin cewa akai shima, baya waske mishi saiya taroshi, basira fikira da zalak'a da kuma wayo, rashin kunyar jarabar da kwatirar duk babu abinda ya rago daga ubanshi, ita kam fatanta bai wuce su jashi a jikinsu ba su raka shi da addu'a, dan ranar mai zuwa tana musu wankin kaya duk sati ya kalla ido cikin ido yace "Habbi ki dinga wanka dan Allah ko kya samu bazawari kema." Ce mishi tayi "To wani bazawari nake nema bayan gaka anan?" Wata dariya ya mata yace "Haba Hajia Habbi, yo ni matar da zan aura ma ai yanzu ne ubanta ke k'uruciyarsa." Sallah magriba kad'ai ta fitar dasu daga gidan basu dawo ba kuma har akayi isha'i, suna kan teburin cin abinci Sayyada ta shigo fa sallama, kai tsaye can ta nufa tana fad'in "Yara ku ce na zo a sa'a?" Hamna ce ta kalleta tace "Su waye yaran?" Kallonta tayi tace "Ku mana, ko ba yarana bane da jikokina anan?" Duka yaran ne suka gaisheta ta amsa da sakin fuska, kallonta Ammar yayi yace "K'aramar uwa daga ina haka a daren nan? Kinsan fa bana son yawon nan saboda ina kishinki." Saida ta kalli Hamna ta bashi hannu tana fad'in "Bamu gaisa ba ma d'an albarka." Da sauri Hamna ta taso ta rik'e hannunshi tace "Aunty bana son iskanci fa, mijin nawa kuma a gabana?" Rik'eta yayi gam a jikinshi ya mik'a mata hannun yana fad'in "Allah sai mun gaisa sai dai ki mutu." Suna gaisawa Hamna ta kalleta sanda take jan kujera ta zauna tace "Allah Aunty idan kika ci amanata saina kasheki a garin nan." Dariya tayi sanda take d'aukar plate zata zuba abinci tana fad'in "Kya kasheni bayan na haifa masa yan uku, ko d'ana?" Ta fad'a tana kallonshi, gyara zama yayi yace "Ai ko da sai na baki kyautar kankana idan kika haifa min yan uku." Hararanshi tayi tace "Ni ko kuma kankanar ta gasken?" Dariya yayi yace "Yo ai kece ta gasken waccen yanzu bogi ce, ke yaushe rabonki da kiga ina shanta?" Shiru tayi dan kar ya b'aro musu kunya a gaban yara, Shureim ne ya kalleta yace "Kakanmu amma dai da yunwa kika shigo gidan nan ko?" Kasancewarshi babban d'a yasa Ammar yace ya dinga zama kujerar tsakiya dake fuskantar tashi kujerar, kuma ko bayana nan babu mai zamanta sai shi, dak'uwa ya masa yana fad'in "Kai uwar tawa zaka ma buru-uba? To da d'anta bai nemo ba ku kanku zaku ci ne." Kallonshi tayi tana murmushi tace "Fad'a masa dai d'ana, ni ai bana da lokacinshi." Murmushi Shureim yayi yace "Gashi kuwa Abba maman nan taka ta iya aika loma baki." Kallonshi Hamna tayi kallon ka shiga taitaiyinka fa, saida ya sunkuyar da kai yace "Yi hak'uri Ummy na daina." Ammar na kallonsu saiya ga wannan sak rayuwarsa ta baya ce zata sake maimaituwa kanshi da kuma d'ansa, dan haka dole ya takawa abun birki tun yanzu, duk da yana so 'ya'yanshi su biyoshi amma fa ba'a komai ba, dan ba zai so suyi wasu halaye nashi ba. Saida suka gama cin abincin yaran suka hau sama inda Hamna tace zata same su suyi karatu, kallon Sayyada yayi yace "Amma dai k'aramar uwa gani na kika zo ko?" Cikin murmushi tace "Eh mana kai da kasan komai d'an albarka." Wani kallo ya mata yace "Samari babu kyauta yan mata babu kud'i, hakane ko?" Da sauri ta kalleshi tace "Wallahi kamar ka sani kuwa, nifa al'amarin mazan nan na bani mamaki." Kallon Hamna yayi yace "Kinga kakana nan ta mayar dani kamar katinta na kud'i, sai dai tace kawo, kawo, kawo kullum a haka." Ba tare data kalleshi ba tace "To idan bance kawo ba wa zan ce wa, ka hanani fita inda zan samu kud'in dole ka zama katina ai." Gwalo ya mata yana fad'in "Hanjin doguwa ce kike ci ta cikin ruwa." Ita ma gwalon ta masa tace "In ma dai ta cikin k'asa ce na ci, mu ai haram d'in ita ke girman da k'assan jikinmu." Kallon Sayyada yayi yace "Kina ji ko uwa, yarinyar nan fa yanzu yar daba ta zama." Tab'e baki Sayyada tayi tace "Karka damu zata daina idan taga ka mata kishiya." Haka dai sukayi hirarsu cikin raha kafin ta mik'e zata koma, jaka sha biyar ya bata yace ta shiga taxi canji saita ci goro, godiya ta masa ta fita ya rakata har k'ofar gidan tare da Hamna, har zai bi bayanta Hamna ta rik'o rigarshi tana fad'in "Ina kuma zaka tafi? Malam muje ciki." Kallon Sayyada yayi yace "Uwa zan kiraki a waya muyi sirri, yanzu d'iyar nan tafi k'arfina." *Bayan sati biyu* Tun jiya dai taga kai da kawonshi ya k'aru sai kaya kaya yake, yau kuma bata san me ya faru ba tun a waya dai taji yana ta fad'anshi, zaune yake kan teburin cin abinci yana daddana wayarshi yana ta sababi kuma, ita dai jera mishi abincin ta shiga yi da duk abinda yake buk'ata k'ala ba tace mishi ba, zuba mishi tayi ta aje mishi gabanshi ta zauna kusa dashi dan ta saba tana kallon tv daga nan. Kallonta yayi ya ga kenan ma babu ruwanta da damuwarsa ko? Cikin masifa yace "Nagode Hamna, dan ki nuna ni mahaukaci ne shine kika aje min abinci wato ina ci ina fad'a ko? Ki ma tambaye ni lafiya abun ya gagara sai ki zuba min ido kina kallo? To nagode." A hankali ta juyo ta kalleshi, yanzu da tace yi hak'uri yace kuma ta ci uwarta ita da hak'urin, sake juya kanta tayi bata ce mishi uffan ba, a hassale ya sake kallonta yace "Ah yayi daidai, yanzu kuma baki da lokaci na ko? Yayi kyau Hamna ki ci gaba da wulak'anta ni son ranki." Mik'ewa tayi ta kalleshi tace "Na d'auke abincin ne har ka gama saboda kar ya huce?" Wani kallo ya mata irin yana so yayi magana amma baisan me zai ce ba, d'auke kanshi kawai yayi daga gareta yana datse leb'enshi dake rawa rawa tsabar fitina bai kuma samu abokin yi ba, juyawa tayi zata shiga d'akinta yace "Ke." Juyowa tayi ta dawo ta tsaya, kallonta yayi yace "Bani ruwa nasha mak'oshi na ya bushe." Cikin kwanciyar hankali ta tsiyaya masa ruwa ta mik'a masa, karb'a yayi yasha ya aje kofin ya kalleta yace "Mak'ogwaro ya fara ciwo wallahi." Cikin nutsuwa tace "Idan baka kiyayi saurin hawan nan ba zaka jawa kanka matsala." Yana ci gaba da kallonta yace "Wai yanzu nan fad'a gareni sosai? To ni ina na samo wannan bak'ar zuciya?" Murmushi kawai tayi tace "Ina ma zakayi koyi da Alhaji, da ka zama mafi dacen rayuwa wallahi." A k'ufule yace "Ke fito fili ki ce Ammar kai masifaffe ne kai mafad'aci kai jarababbe ne, anje anyi d'in to inba tab'aka akayi ba ai haka kawai ba kayi fad'a ba." Juyawa tayi ta bar masa wurin dan ta lura da tsiya ne take so ya jata ta biye masa k'arshe ya turmusheta kuma ya d'inketa da kanshi, sauk'inta d'aya ma yanzu ciki dake gareta bai cika mata wannan hawan k'awarar ba. Ko da ya ga zata shige d'aki ya d'auki cokalin abinci yana bubbuga teburin yana fad'in "Yeeee, ku dubi matar dake kallon mijinta masifaffe, an daiji kunya wallahi, kuma sai nayi mata uku a lokaci d'aya naga wanda ya isa ya hana ni." Ko juyowa ba tayi ba har ta shige tana jin shi yana ta sambatunshi, saida ya gama yayi wanka ya shirya zai fita ya same ta a d'akin, bai kai ga mata magana ba kuma wayarshi tayi k'ara, yana dubawa ya ga Sayyada ce, tun ranar data zo ya kirata sukayi magana kan ranar haihuwar Hamna da zata zagayo yace yana so ya shirya mata party a gida, shi kuma yana so ya mata bazata shiyasa ko da ya ga kiran saiya d'auka yace "Oui zan sake kira idan na fita." *Mata muke fa, kowane yare na maza ganeshi muke cikin sauk'i* Daga jin yace zan kira bai ce zan kiraka ba kenan ba namiji bane, sai kuwa Hamna ta sauko daga kan gadon tayi kafar da wayar ta d'ora a kunne tana fad'in "Hello! Hello." Fizge wayar yayi yana fad'in "Ke me yake damunki ne?" Cikin d'aga murya tace "Abinda yake damunka, Ammar amana ta kake ci? Wace yar iska ce ke kiranka har cikin gida?" A hassale shima yace "Wai ke kullum sai ki ce yar iska, to duk matan duniya yan iska ne? Ke ma fa macece saiki dinga kiransu da yan iska?" Cikin b'acin rai tace "Saboda yar iska ce kawai zata kula min miji." Kallonta yayi yace "Fito kai tsaye ki ce nine d'an iskan mana, idan ban kulasu zasu kulani ne? Kinga kenan nine kike so ki zaga dama." Wayarshi tasa hannu zata fizgo tana fad'in "Na ga wayar to." Hannu ya d'aga kamar zai mareta yana fad'in "Idan ban mareki ba Hamna kice Allah ya tsine min, ke bari gani ina k'yale ki fa." "To ka da ka k'yale ni d'in ka kashe ni." Zaune tayi kan gadon ta fashe da kuka tana dafe cikinta tana fad'in "Daga yau zan fara addu'a Allah ya cire min sonka, tunda dai dan kaga ina sonka ne kake wahalar dani, me ye gare ni da ba zaka iya rayuwa dani ni kad'ai ba? Kullum tunani na shine yanda zan faranta maka amma kai ba haka ba." Da sauro ya zauna kusanta ya rumgumota a jikinshi yana fad'in "Kai kai kai Hamna, karki fara wannan addua'r dan Allah, kinsan kuwa yanda nake ji idan kina wannan sababin akan kishina? Wallahi karki tona raina kiji farin cikin da nake, kamar yanda nake kishinki nake jin zan iya komai haka nake so ke ma kiji a kaina, kiyi hak'uri kinji." Kaallonshi tayi tace "To wacece ta kiraka yanzu?" Wayar ya fito da ita ya mik'a mata yace "Duba ki gani." Dubawa tayi kam ta ga sunan Sayyada, kallonshi tayi tace "Sayyada ce ta kiraka ba zaka iya magana da ita a gabana saika fita, wani abu ne tsakaninku?" Da sauri ya dafe k'irji yace "Ni? Wallahi babu komai, ki yarda dani." Kallonshi tayi da kyau tace "Allah yasa haka, amma ka sani Ammar duk ranar dana ji wani abu ya fito tsakaninku mai kama da soyayya ko aure saina maka sabon yanka." 😂😎 Zaro ido yayi yasa tafukan hannayenshi ya rufe baki yana fad'in "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, Hamna gaba d'aya fa anan mazan suke." Ba alamar wasa tace "Saboda nasan anan suke d'in ai shiyasa suke alamta maka daka kalli matar da ba taka ba ai." Tab'e baki yayi yace "Gwara ki kashe ni ai da ki tab'a min kayan aiki na." Murmushi tayi tace "Ai saboda su d'in ne zakayi sha'awar k'ara aure." Kallonta yayi yace "Ke ma ba zaki iya zama dani ba ai idan da bana tsoratarwar nan." Cike da tabbaci tace "Zan iya mana, kuma ita Sayyada ai zata iya tunda yar uwarka ce." Mik'ewa yayi yace "Ke babu aure tsakani na da ita fa." Ita ma tsayen ta mik'e tana fad'in "Inji wa yace? Ai ko su Abba akwai aure tsakaninsu da ita bare kuma kai." Ba tare daya kalleta ba yace "Ni ai Sayyada ma bata cikin tsarin irin matan da nake so, ni nafi son masu manyan cinya da mazaunai yanda idan na shiga zaiyi luf abuna." Kallon sama da k'asa ta mishi tana fad'in "Kace haka mana, kafi son irina yanda zaka ji dad'in b'arka mu kana d'inkemu." Dariya yayi yace "Ai da kinga na miki d'inki to kin b'ata min rai ne." "To me yasa ba zaka hukunta ni ta wata hanyar ba sai wannan? Kana so ka lalata ni ne?" Saida ya jawota jikinshi yace "Babu abinda zai faru, kayana mallakina da ni kad'ai ke da hurumin shigarsu, nasan yanda zan ci gaba da tafiyar dake." A daren bayan ya fita Sayyada ta zo tare da masu cake d'in da aka bawa suyi, shi kad'ai ma abun birgewa ne kamar kayi ta kallo, ga kyaututtuka daya mata na bazata da gigita tunani, tayi farin ciki sosai tare da mishi godiya. *Rayuwa dama haka*, duk son kwalliya da k'walisar Hajia tsufa ya kasa barinta ta ci gaba, inda yanzu ta fara rud'ewa wani abun idan tayi sai an kalli juna, ita da Husseina zamu iya kiransu da tsofi masu taurin rai, dan har yanzu suna nan a cikin gidan ana ta damawa dasu ana kuma fama dasu, yanzu Ummy ce kawai mai fad'a a ji a gidan a cikin mata dai, komai sai ace Ummy Ummy, sai dai kuma yanzu gidan babu hayaniya kamar da, dan tunda Ammar ya tashi kowa ya k'wallafa rai yana so ya tashi, a hankali duk sukayi nesa dasu sai dai su kawo musu ziyara. Har yanzu Amar na fama da Umaimah wacce ta kasa fahimtar inda duniya tasa gaba, sai dai farin cikinshi d'aya Farisa, babban sake da tayi shine barin Farisa ta fahimci irin zaman da suke, daga sanda ta gane saita d'auri niyyar faranta masa, kuma akan haka take yanzu, in dai ba larura ta yau da kullum ba bata yarda ya sameta da k'azanta ba ko da ba ranar aikinta bane, kullum cikin gyaran gidanta da jikinta take, shima kuma yanzu yayi wuri ya aje Umaimah idan ta fara bala'i saiya bar mata wurin, haka ya zage damtse kamar yaro shima yana ta kwasar soyayyarshi da ita, baya jin nauyi ko k'yashin yi mata abu ko million nawa yake, haka zaman nasu ke tafiya farin ciki a hannun dama bak'in ciki a hannu hagu. Su Junaid ma da Salma da kuma Jibril da Jamila da Zeinab da Jamil duk dai rayuwa ce irin ta yau da kullum, yau farin ciki gobe bak'in ciki sai dai farin cikin shi yafi yawa, sab'ani ne da dama dole a same shi tsakanin mutane bare kuma ma'aurata. B'angaren Amarya Huda ma tana farin cikin zamanta, kullum suka d'an samu sab'ani ko k'arami ne sai yace karta fad'awa tonton Ammar, dan ya samu labarinshi shi har ga Allah tsoronshi yake, da haka Huda ke tak'ama tana murza rayuwarta ita ma. Matsalar mahaifiyarta dai ce ke d'an mata cikas wani lokacin, duk da har yanzu a dangin mijinta babu wanda ya kalleta yace yar karuwa, amma tana jin kunyar kasancewarta yar Mari dan babu shiriya a gabanta, ta zo gidanta sau d'aya amma saida ta fito fili ta fad'a mata ta dinga canza shiga indai har zata zo gidanta, irin bala'in data gani a ranar kamar zata cinyeta d'anya, ita dai bata biye mata ba tayi ta gama sannan tace ta bata kud'in mota, ko da ta bata ta tafiyarta ko sallamar arzik'i basuyi ba. Gambo duk da baya kan muk'aminshi amma har yanzu ana damawa dasu a siyaya, Hajia tace ya dawo amma ya kasa dawowa saboda ya saba zaman can, saidai ya zo yayi kwanaki har satittika ma sannan ya koma, Aissata ma na nan banda buga mulkinta babu abinda take yi, shiyasa aka ce *wata shari'ar sai a lahira*. A k'arshe dai ta samu mijin aure bayan ta kwashe shekara *talatin* cir a duniya, kasancewarta mai k'aramin jiki yasa ba zaka ga shekarun a jikinta ba sai a fuska, Sayyada kenan (my besty na), Hamna sun shiga hidima sosai ba kama hannun yaro inda ta d'auki nauyin gyaran amarya da kanta. Yau ake kamun amarya, kuma ta rok'i Ammar ya kaita yace babu inda zata je da tsohon ciki, saida ya fita ya bar gidan ganin a gidansu Hajia ne sunfi kusa da plaza kawai ta shirya tare da Ameera ta tuk'a motar Ummy suka tafi. Bata tab'a tsammanin yasan mijin da zata aura ba dan bai tab'a fad'a mata ba, bata kula da motarsa ba a filin wurin saida ta shiga can ciki, hangoshi tayi cikin abokansu suna ta hira, rik'e Ameera tayi a hankali ta shiga juyawa da nufin su koma, saida ta sauka kan matakala ta tsaya tana sauke ajiyar zuciya, kallon Ameera tayi tace "Beby Allah ya taimakemu bai ganmu, yau da cire mana wando ta kai." Dariya Ameera tayi tace "Ummy mu tafi to, ni ke nake tsoro ma yaje gida yayi ta miki masifa." Dariya tayi ta kama hannunta suka sauka, saida ta kama murfin k'ofa zata bud'e ta shiga taji message ya shigo wayarta, ko da ta bud'a message ne kamar haka. _"Mrs Ammar Gaga, tun kafin ki shigo numfashina ya canza salon bugawarsa, hakan ya tabbatar min kina kusantowa gareni, taya kike tunanin na barki sakaka da har zaki iya min satar hanya, kuje gida sai na zo zamu had'u, ki kula da kanki."_ Lahaula, shikenan ta *faru* ta *k'are*, kallon Ameera tayi tace "Baby ya ganmu fa." Zaro ido tayi tace "Lah Ummy mun shiga uku, yau zamu sha bulala a gida." *_Washhhhhh Allah, na tsaya iya nan, dramarsu kullum aukuwa take, kunsan waye Ammar nasan kunsan me zai faru idan ya koma, baya barin ta kwana kamar yanda baya mantuwa da yafiya, baya bawa mak'iyinsa baya sai dai ya tareshi duk a rugumtsuma, see u Ammar, yan matanka na nan lodi lodi birjik suna jiran amsar amincewa buk'atar aurensu daga bakinka, ni ban tab'a jarumi mai farin jini irinka ba ma, ga kuma santaleliyar k'anwa daka samu uwar yarinyata wacce ke shirye da take bayanka bata son b'acin ranka, ni kuma uwar d'akinka duk muna bada gaisuwa shugaba. Auntynmu Hamna gaisuwa gareki ta musamman, masoyanki na nan tare dake, Allah k'ara had'a kanku tare da baki hak'uri da juriya na zama da yayan uwar jaririyata, kishiyoyinki ma suna gaisheki tare da rok'on alfarmar ki barsu su shigo suma su samu nasu rabon d'inkin.🏃‍♀️🏃‍♀️🏃‍♀️*😂 *Alhamdulillah* *Alhamdulillah* *Alhamdulillah* *Yan uwa mun kawo k'arshen BADAK'ALA, sai mun had'e a SALAHADEEN da SARAH*