An dauko wannan littafi daga shafin https://novels.com.ng ku ziyarci shafin na https://novels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348062902098 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://novels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348062902098 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT : *DANDANO DAGA ABARI YA HUCE* *MAIRO A GIDAN YAYA HABIBU!!!* © *Sumayyah Takori* Litinin babbar rana, ko bature yana tsoronki. Habibu ya yi shirin ofis cikin _suit_ din ma'aikatan bankin _Barclays_ , da jibgegiyar rigar sanyi, hand-socks da leg-socks, yana so zai fita aiki. ga yara sunyi shirin makaranta tsaf, misalin karfe bakwai daidai na safe. amma babu hanya, domin kuwa tashi sukayi suka tarar kankara ta rufe kofar gidan ruf, da tagogi bakidaya. Dina ma ta fito cikin nata shirin cikin kayanta na lauyoyin banki, tana ta korafi akan 'snow'. Dole Habibu ya fiddo waya ya kira ma'aikatan sare kankara, nan da nan suka zo cikin minti goma, suka bambare kankarar sannan suka samu hanya suka fita. Mairo ta fito daga dakinta ta yiwa sanyi mugun shiri, baka ganin komai nata sai shacin kayatacciyar fuskarta kai ka ce balarabiyar *Morocco* ce. Tasa yaran a gaba suka fito tana dauke da little Mairo, suka zo bakin hanya suka tsaya tana rike da hannayensu, tsayuwar minti biyar sukayi motar makarantar su ta iso ta sanya su ciki suka tafi, suna daga mata hannu itama tana daga musu. Kasancewar ita bata da karatu a yau sai ta kama hanya cikin nutsuwa ta koma gida. ( _Wannan shine tsarin rayuwar gidan Yaya Habibu a kullum. Duk wayewar gari kowa abinda yake yi kenan)._ Mairo na karantar Zamantakewar Dan adam (Sociology ) a jami'ar Michigan (Michigan State University) tun bayan dawowar ta gidan Yayanta Habibu. A yammacin ranar tana zaune a _study-room_ da farin gilashin karatu a idanunta tana nazarin littafin 'Haralarambus and Holborn ( _Sociology_ , _Themes and Perspectives_ ) domin wani assignment (aikin gida) mai matukar wuya da aka basu akan *hedonism* zasuyi _submitting_ a washegari. Aunty Dina ta murda kofar ta shigo fuskarta dauke da murmushi, sassanyan kamshin ta na turaren (yves saint laurent) shi ya fara bakuntar hancin Mairo kamar koyaushe, Dina mace ce mai darajja kamshi a jikinta ta dade da sanin wannan. Ta ja kujerar dake fuskantar Mairon ta zauna sannan tace "Mairo dan rakiya nake nema, London zan je gobe ko zan samu ki raka ni?"Mairo ta shiga girgiza kai da sauri "inada aiki mai yawa a makaranta goben, kuma zanyi submitting assignment dina, me zaki je kiyi?" Ta ce "kallon 'film-fare award' na wannan shekarar, gara in gani _vivid_ fiyeda a talabijin nafi gane komai. Tun wancan satin ake ta sanarwa za'ayi". Mairo bata san kallon Indian na Aunty Dina ya kai matsayin haka ba, da zata ni ki gari kasa-ya-kasa tun daga birnin Michigan har babban birnin Birtaniya don kawai ta ga GALA! Da sauri tace "sai kin dawo. Ni kam, bazan samu zuwa ba". Habibu da taya bera bari ya yankowa Dina tiket ta tashi a washegari, gidan ya saura sai su kadai. Tun safe Mairo na makaranta tana fama da ayyukan gaban ta itada kawarta Ir'eesh Tawheedah 'yar asalin kasar Somalia. Bata dawo gida ba sai yamma lis, ta tarar tuni Yaya Habibu ya riga ta dawowa. Zaune suke a falon shi shida yaran suna aikin makaranta yana nuna musu. Mairo tayi sallama ta shigo suka yi tsalle suka daneta suna yi mata "oyoyo". Yaya Habibu ya daga ido ya kalle ta yana mamaki cikin ransa wai wannan Mairo ce, MAIRON GURIN-GAWA, MAIRON-HURE! Abu daya ya tuno a wannsn lokacin yayi murmushi (goruba daga kan bishiya a kauyen GURIN-GAWA) ya ce "Mairo 'yan makaranta.... Mairon Dina. ... Mairon Yaya Habibu...!" Ta yi dariya har fararen jerarrun hakoranta suka fito. Kirarin da yake mata kenan idan ya so nishadi. Ta wuce dakinta rungume da jakarta don ta kimtsa. Bayan tayi sallar magriba tayi wanka ta canza kayan jikinta ta fito falon ta zauna tare dasu. Zuwa can Yaya Habibu ya fito daga dakinsa cikin shiri, sai kamshi yake. Ga dukkan alamu cikin sauri yake. Ya dube tayace "maza a shirya dinner, amma _African-Dish_ . Inada babban bako anjima kadan. Babban abokina Amiru zai sauka yanzunnan daga Washington D.C zan je filin jirgi na dauko shi". Yadda yake maganar cikin rawar jiki kadai zaka fahimci wannan bakon mai muhimmanci ne da matsayi na musamman a gareshi. Ba tun yau ba Mairo na jin sunan Amiru a bakin Yaya Habibu da Dina. Zata iya cewa rana bata fitowa ta fadi wani cikinsu bai ambaci Amiru ba. Ta amsa da ladabi "toh, sai kun iso". Yana fita ta mike ta nufi kicin, Lynder na goge-goge ta bata hanya ta wuce, ta bude _deep-freezer_ tana tunanin me zata dafa musu? Daga bisani zuciyarta ta tsaya akan tuwon shinkafa miyar danyar kubewa tunda dai suna da Okora (danyar kubewar gwangwani). Nan da nan ta dora sanwa, tayi amfani da _dried fish_ da _mushroom curry_ cikin miyar, duk kicin din sai ya dau kamshi. Sunada zobo, don haka ta tafasa shi ta tace, ta markada abarba ta hade da zobon da fulebo din abarba ta juye a _jug_ ta sanya a firji don ya yi dan sanyi ba tareda ta sanya sukari ba. Ba tun yau ba ta san Yaya Habibu da son Danwanke, kai shi duk wani abinci ma na Africa to ya bi bayan dan wake. Don haka nan da nan ta jika kanwa ta kwaba ta jejjefa cikin tafashashshen ruwan zafi, cikin dan lokaci ta kammala komai. ****** Ta kashe wayar ba tareda ta baiwa Nabilah amsa ba. Jikinta a sanyaye matuka, maganganun Nabilah kullum irin na Anty Dina ne, ko maiyasa? Alhalin basu san juna ba, basu taba ganin juna ba ko a hoto, balle tace sun hada baki ne suna _sharing idea_ don su kalubalanceta! Dai-dai lokacin taji shigowar Yaya Habibu da bakonsa. Da alama ba su biyu bane don tana jin muryoyin maza daban daban. Ta sake kudundunewa a cikin bargonta sama-sama take jiyo tashin muryarsu anata turanci kamar tashin duniya. Kira ya shigo wayarta, daga kwance ta mika hannu ta amsa a kasalance. Dina ce. Tace "yaya kuke Mairo? _Hope_ ba matsala, ina nan tahowa gobe insha Allah, mai zan sayo miki?" Mairo ta ce "munyi kewarki ne kawai Anty, duk gidan ba dadi da baki. Bana bukatar komai sai dawowar ki lafiya". "Nima haka Mairo, ji na nake kamar nayi shekara ban ganku ba. Me ya samu wayar Habib ne? Na kasa kama shi". Tace "yana falo, yayi baki ne". "Su waye?" Mairo ta ce "Na dai ji yace Amiru ne" Dina tace "wow! Amiru yau a gidanmu? Maza kaiwa Habib wayar inason magana da shi". Ta mike rike da wayar ta fita, shaf ta manta ko kanta bata rufe ba tsabar yadda Dina ta matsu tayi magana da mijin nata, a haka ta isa falon. Ta karasa kusa da Habibu ta mika masa wayar. Juyowar nan da zatayi sai idonta cikin na Amiru, wanda ke zaune gefen Habib cikin _Italian Suit_ bakake wul, ya sassautama wuyanshi ruwan tokar _tie_ dake jikinshi. Suka samu kansu cikin matsananciyar faduwar gaba a lokaci guda. Ga ita Mairo, kwarjini ne da kyawun Amirun ya haifar mata da faduwar gaban. Amma ga AMIRUN, bazan iya cewa ba! Habibu yace "Amiru *meet my beloved sister MAIRO* , da nake baka labari...". Yana mai kokarin saita lumsassun idanunsa akan Habibun, don kawar dasu daga nacewar da sukayi akan Mairon yace "itace Mairon??? Mairo zo mu gaisa....". Amiru dai Hausa yayi, amma wani _accent_ ne da Mairo bata taba jin mai gardinsa cikin kunnuwanta ba. Kamar yadda bata taba ganin mutum mai kyau da kwarjininsa ba, ilhamomin dake tare da shi bata taba haduwa da mai irin su ba! Wannan shine AMIRUN Yaya HABIBUN??? ( _The beginning of everything_ kenan) ***** Mairo data koma daki kwanciya tayi rigingine cikin nadama. Kai tsaye ka dubi kwayar idon mutum mai kima kamar Amiru, kace baka sonsa ai ya zama wulakanci da cin fuska. To amma ita a ganinta daidai tayi, don bata iya karya ko yaudara ba. Amma dai duk da haka ta san bata kyauta ba. Saidai a ganinta gara hakan, da dai tayi irin auren da zuciyarta ta raya mata akansa. Dina tayi sallama ta shigo tana fadin "tashi, abincin da kike gudu ne na biyo ki da shi. In dai Amiru ya dade da barin gidannan. Ta tashi ta zauna sosai ta karbi farantin ta soma ci. Dina na kallonta, can kuma tace "Mairo me kika ce da Amiru ne? Ya shigo cikin walwalarsa, ya fita a yanayin da bamu taba ganinsa a ciki ba. Ina laifin wanda ke son ka?". Ta cira kai daga cin abincin tamkar wadda aka katse wa gudun jini a cikin jikinta, sai kuma ta sunkuyar. Can kuma ta dago ta dube ta tace. "Yana magana ne kan wai yana so na, so kuma na aure, yana burin na zama uwar iyalinsa. Nikuma na gaya masa kai tsaye cewa "bana son sa!". Dina tayi murmushi, daga jin kalaman Mairo da yanayin maganarta kasan kuruciya na dawainiya da ita. Cikin sanyin murya tace "sabida me ba kya son nashi Mairo? Gashi kyakkyawa son kowa kin wanda bai samu ba, gashi da dimbin ilmi kamar Yaya Habibun da kike cewa yana burge ki. Yanada matarshi baturiya zallah amma ya tsallakota yazo yace ke Mairo yana son ki. Zai iya rabuwa da ita saboda ya aureki. Gashi da kirki ga addini, ke kuwa Mairo me kike nema a da namiji da ya wuce wannan?" Sai Mairo tasa kuka, ta kwantar da kai a cinyoyin Dina, ta shiga kuka mai tsuma zuciya. "Na kasa mance *Uncle Junaidu* ne Anty Dina! Na kasa mance dimbin alherin da yayimin a rayuwa. Shine tsanin duk wani matsayi da matakin dana ke kai a yau. Idan na auri wani ba shi ba na ci amanar sa.......!" Dina ta katseta "akwai hanyoyi da yawa da zaka sakawa mutum Alherin da yayi maka ba dole sai ta hanyar aure ba. Misali shine ki dinga bin shi da kyakkyawar addu'a ba tareda shi din ya sani ba. Wannan addu'ar Ubangiji yayi alkawarin karbar ta Mairo. Kada ki yi mamaki zuwa yanzu shi Junaidun ya samu wadda yake so ya aura ya manta da ke. Ni na kasa gane kan wannan soyayya da kike yiwa Junaid maras dalili. Kin ce bai taba cewa yana son ki ba! Kince ba kuyi alkawarin aure ba! Kince ya san gidan Baffa amma bai nemeki ba! To Mairo gaya min wace hujja gareki da zata tabbatar da cewa yana son ki? Bakisan akwai masu taimako sabida Allah ba? Ba don a aure su ko a saka musu da soyayya ba? Haba Mairo, kiyi tunani mana, kiyi amfani da hankalinki, ki so mai son ki a zahiri da badini. Kiyi aure saboda Allah da raya sunnar Ma'aiki amma ba don abinda zuciyarki ta afu a kai ba. Ina tabbatar miki Amiru in kin nutsu, kin bude zuciyarki a hankali zaki so shi wallahi har ma fiyeda son da kike ma Junaid. Iyakar soyayya ta gaskiya kin yiwa Junaid, ko baki aure shi ba Allah ya shaida! Yayi alkawarin sanya masoyan gaskiya da suka mutu ba tareda sun auri juna ba a gidan aljannah. Ina tunanin Junaid yayi abin nan ne da hausawa ke cewa ABARI YA HUCE SHI KE KAWO DA RABON WANI!" Ta dubi Dina da sauri har tsakiyar idanunta tace. "Idan hakane Aunty Dina, kema kin yarda Uncle Junaid yana so na, furtawa ne baiyi ba kamar yadda _Inna ta_ da Nabilah ke cewa???" Gyada kai Dina ta yi. "EH, yana son ki, amma ya bari YA HUCE! Don kuwa a zahiri babu wata mu'amala ta mutunci da tausayi tsakanin mace da namiji sai 'SOYAYYAH'. In ma mutuncin ne da farko, to daga baya rikidewa yake ya koma soyayya. ... Ke dinnan Mairo har wata soyayya kika sani ko halarci? Wallahi HALACCI kike yimawa ba soyayya ba. Amirun shi kike so da gaske; na gani a kwayar idon ki, na gani a gangar jikinki. Kina jin abubuwan da kike ji kan Amiru a Uncle Junaidun? Kina neman Junaid ya aureki ne don ya tallafi rayuwarki a wancan lokacin da kike neman matallafi ido rufe, amma ba don kinsan hakikanin me aure ya kunsa ba. Mairo kinaso ki ramawa Junaid halaccin da yayi miki ne ta hanyar 'aure' don da shi kika saba, ya sanki, kin san shi, a tunanin ki wannan shine karshen soyayya, to ba shi bane! Soyayyar aure daban take, Allah ke hada ta, kuma bata fassaruwa. Ita zuciya an halicce ta ne da son mai kyautata mata, wannan shine tsakaninki da Junaid ba soyayyar aure ba! Idan kuma mata sun fara zuwa neman aure ne to sai muyi shirin tafiya Kano, unguwar Galadanchi gidansu Uncle Junaidu, mu nemeshi mu kai kudin aure... mu gaya masa yadda kike son shi, har kina duban tsakiyar idanun masu son ki da aure na hakika kina gaya musu ba kya son su. ......sabida kawai kada ki ci amanar soyayyar shi da ya baki a makaranta. ......" . Ala dole ta murmusa, ta san _zambo_ ne Dina take mata. Duka wannan bata lokacin da yawan bakin da Dina ta share tana bayani, ba duka abinda tace ne Mairo ta yarda dasu ba. Ta dauki Dina a matsayin mai campaign ga AMEERU! Sabida shi ta sani, shine mai irin tsarin rayuwar su. Bata san komsi game da rayuwarta ta baya ba, batasan wanene Uncle Junaid a rayuwarta ba. Ita kudin Yaya Habibu ma tsoro yake bata balle na Amirun da ta ji suna cewa yana _World Bank_ karewar _Barclays_ . A karkashin inuwarsa rayuwar Habibu ta ginu bakidayanta. Shi ya maida Yaya Habibu ko me yake a yanzu. Ta yarda ta hakura da Uncle Junaidu sabida hujjoji kwarara da kowa yake gaya mata. Hatta Nabilah tace da ita "lokaci yayi da zata manta da Uncle Junaidu tayi aure". Ta dubi irin auren da ita tayi, amma daga baya ya zame mata ALHERI. Don yanzu ba abinda take so a duniya sama da Ismael kuma shima hakan har ga albarkar haihuwa. Ta sauke ajiyar zuciya ta koma ta kwanta bayan fitar Dina. Ta ja bargo har kanta ta kudunduna. Bacci take so ta yi amma ya ki zuwa. Al’amuran na neman tarwatsa mata kwakwalwa tareda wargaza mata tunani bakidaya. Tana so ta yarda da Dina, halaccin dake zuciyarta na karyata Dina. Amma abubuwan da ta zano ai duk haka suke; zata je neman auren Uncle Junaidu ne??? Ko kuwa haka zata kare a zaman jiran *tsammanin warabbuka* ??? Zata iya cigaba da zaman jiran ranar da uncle Junaid zai nemeta, ya bayyana mata soyayyarshi, ya bata uzurin da ya hana shi yin hakan a lokacin da ya dace daga nan har gaban abada! Amma bazata iya jure bukatar gangar jiki da zuciyarta ba irin na kowanne lafiyayyen dan Adam. In hakane aure ya zama dole a gareta domin kare kanta daga _zina_ , da sauran ayyukan alfasha, cikar mutunci a idon duniya da karuwar matsayi a fadar Ubangiji. Wayarta dake karkashin filo ta soma dan kidi mai sanyi, alamar shigowar sako (text ). Cike da mamakin wanda ya yo mata sako a daidai wannan lokacin karfe biyu na sulusin dare agogonsu na can ta mika hannu ta lalubo wayar ta danna. Bata san lambar ba don kuwa bakuwa ce, ga abinda ke rubuce; ".......... _When life changes, and we go our separate ways, you will still be in my heart till my dying days...... my world has never meet a person like you!"_ (A yayin da rayuwa ta canza ni da ke muka bi hanyoyin mu mabambanta (muka rabu) zaki cigaba da zama a xuciyata har karewar numfashi na. Duniyata bata taba haduwa da mutum irin ki ba). Haka ta sa sakon a gaba tana ta karantawa har akayi kiran Assalatu. Don ta tabbata ba kowa bane; Amiru ne. Duk da bai saka suna ba ko wata alama mai nuna shi din ne. Allah sarki! Har YA HUCE ne? Tana so ta bashi amsa bata san me zata ce masa ba. Da safe take nunawa Dina a kitchen, ta karanta tayi dan miskilin murmushin nan nata. Tace "ke kuma kika ce me?" Ta zumburi baki "ni ko kula sa ma na yi?" Dina tayi dariya tana kwaikwayon muryar ta tace "Haba Mairo! Yi hakuri ki dan kula sa. Kin ga shi yayi fushin amma ya sauko, sabida ya fahimci Mairo ba sonsa bane bata yi, kawai ita din mai *amana* da *rikon alkawari* ce". Tayi murmushi har kumatunta ya lotsa. Dina kam akwai shegen wayo, kanwa ce uwar gami. Tace. "To me zan rubuta???" "Ki ce kawai yazo yayi _joining_ dinmu _breakfast_ ". Mairo ta rubuta ta tura. Amsar da ya bata ta sa ta yin murmushi, domin ya ambato rabin ranta. "A'ah kirawo JUNAID......" " He's far away....!_ " (Amsar Mairo). "And I'm not closer too.... I'm far away either, and I will not come back. On my way to Detroit-Metro". Hankalinta yayi mummunan tashi. Saboda ita ne Amiru zai bar kasar da haihuwarsa ne kawai ba'ayi cikinta ba? Da sauri ta jefar da wayar. Da gudu tayi daki ta dauko mukullinta. Dina na kira amma bata juyo ba take fadin. "Shima zai tafi ya barni, kamar yadda Junaid ya gudu ya barni. Bayan sun kimsa min soyayyarsu. Banaso in samu wannan _heartbreak_ (karyewar zuciyar) a karo na biyu". Dina tace. "Bi shi Mairo. Shine ZABIN ALLAH!!!" Gudu take shararawa a kan titin da zai kaita _airport_ din Detroit. Cikin kankanuwar motarta *GMC Terrain.* Hawaye na sauka akan kundukukinta. Da gaske Dina ta ke; wannan itace SOYAYYAH! Da gaske Dina ta ke Amiru shine ZABIN ALLAH! Da gaske Dina ta ke da tace ta kama mai sonta, ta rabu da *JIRAN TSAMMANIN WARABBUKA!* Ta karbi *soyayyah* a hankali zata rikide ta zama *kauna* . To ga shi soyayyar ma zata gudu ta barta da tsammanin warabbukanta wanda bata fata. .........................!!! Koda Ta iso airport din ko kulle motar bata yi ba, a jikin motar ta bar mukullin. Da gudu ta shige cikin _reception_ tana dube dube. Babu Amiru babu ko mai kama da *AMIRU* ! Ta karasa _terminal_ bayan ta hankade ma’aikacin dake kokarin hanata shiga. Daidai sanda anka rufe kofar jirgin ( _Lufthansa_ ) wanda zai tashi zuwa kasarmu mai dimbin albarka. Ba da jimawa ba kuma ya soma ruguginsa mai gigitarwa bisa kwaltarshi, kafin ya daidaita sosai a sararin samaniya. Mairo ta durkushe anan tana kuka. Kukan da ta dade batayi irinsa ba tun bayan rashin BABANTA da INNAR TA. Fita yake tun daga karkashin zuciyarta. Amiru ya tafi tareda dukkan farin cikin data samu cikin *Michigan* wanda Yaya Habibu ya dade kafin ya assasa. Bai shigo rayuwarta da sauki ba ashe! Ashe ya shigo ne ya kara rusa komai. Ya tafiyar da sauran karfin zuciyarta. Ya dawo da rayuwa *unbearable* kamar kamar uncle Junaidun? Me yasa ita bata da sa'a a soyayya komai kankantarta??? Ji tayi kamar an tsugunna a gabanta, kamin ta dago kuma an kai hannu a hankali an dafa kafadarta. A sannu ta dago idanunta jage-jage da hawaye, don ganin ko wanene wannan??? *A BARI YA HUCE* . ...... Littafin *_Sumayyah Abdulkadir Takori*_ _Wannan littafi tukuici ne ga masu sha'awar ganin rubutun TAKORI a yanar gizo. Ga mai son cikakken labarin (book 1-4) ya biya N1000 ga wannan account number_ *Sumayyah K Kabara* *Zenith bank* *2089357770* _Sannan sai ya turo screenshot zuwa 07030137870_ NAGODE 7/28/21, 10:59 AM - Buhainat😝: KAUYEN GURIN-GAWA, 1988 Gurin-gawa karamin kauye ne mai tsohon tarihi da ya kunshi al'umma masu sana'o'i daban-daban, amma duka tushensu daya. Galiban malamai ne da manoma, kuma kauye ne da manyan malaman da a halin yanzun suka barwa duniya abin da ba za a mance da su ba suka fito. Gurin Gawa na nan cikin karamar hukumar Kumbotso, yankin Fanshekara ta jihar Kano. Karamin kauye ne, wanda ya samu tallafin gwamnati ta hanyar wutar lantarki, ruwan sha mai tsabta, da takin zamani, wanda ke taimaka musu kwarai wajen bunkasa harkar nomansu. Akwai sanannen hadin kai tsakanin al'ummar garin mazansu da matansu. Sai dai kuma babu titi mai kyau a Gurin-Gawa. Idan mota ce zata shiga kauyen sai ta yi futuk da kura, mutanen cikinta sun gwaggwara kawunansu sabida rashin kyawun birjin. Duk da haka wannan bai hana al'ummar cikinta jin dadin zamanta ba, motar haya ba ta shiga cikin kauyen, sai dai ta aje ka a titin ka hau achaba ko bayan akori-kurar Rake ta mutanen garin ka karasa ciki. Don haka da wuya ka ga mutanen birni na shiga kauyen, don a ganinsu ba su ga mai zasu tsinto cikin wannan kalataccen kauyen ba. Samarin garin Gurin-Gawa kan fita cikin Fanshekara da wajenta domin neman kwabo, ta hanyar ga-ruwa, sayar da rake, dukanci, dako da sauransu. Don kalilan ne suka damu da makaranta wadda dama idan dai ta boko ce, to ba a zancenta cikin garin Gurin-Gawa. Makarantun allo da na Buzu su ne Allah Yai yawa da su a garin. Malam Bedi, yana daya daga cikin dattawan garin Gurin Gawa, haifaffen nan ne iyayensa da kakanninsa. Sana'arsa shi ne noma, yana da gonar rake da gyada, sannan yana nome dankalin Hausa, makani da gurjiya. Bedi da matarsa Hure, fulanin Gurin-Gawa ne na usul. Mutanen kwarai ne da duk Gurin Gawa ba wanda bai sansu ba, tare da yi musu kyakkyawar shaida. Babban dansu shi ne Habibu, wanda tun yana karami Malam Bedi ya dankawa kaninsa mai bi masa a haihuwa ya ke taya shi sana'ar fataucin goron da yake yi daga Shagamu zuwa Kano, wanda daga baya shi Habibu ya shiga makarantar horas da malamai (SAS) tun daga wancan lokacin kuwa ya koma Kano kwata-kwata. Shi da Gurin-Gawa sai dai yazo da yawo idan ya zo gaida mahaifansa wanda yakan dauki dogon lokaci bai yi hakan ba. Su ma su Malam Habibu ba su wani damu da shi ba, don ba wata cikakkiyar shakuwa ce a tsakaninsu ba. Duk wani burinsu na duniya yana kan 'yar autarsu “MAIRO”, wadda ba su samu ba sai bayan shekaru sha takwas da haihuwar Habibu. Don haka idan ya zo a tura mai kujera ya zauna, ana lale da shi, idan bai zo ba ma falillahil hamdu. Inna Hure ce duke tana faman firfita wutar iccenta, domin ta samu ta kammala abincin rana kamin Malam Bedi ya dawo daga gona. Idanunta sun yi jawur sai zuba suke, ga dukkan alamu irin azababben itacen nan ne Allah Ya hadata da shi. A gefe 'yar lelen ce zaune bisa tabarma tana dandasawa 'yar bebin karanta kwalliyar juma'a da wani tsalelen yankin yadin mamar-mamar da ta tsinto a shagon tela. Ta daga 'yar bebin tana cillawa tana cafewa tana wakarta cikin nishadi, ga dukkan alamu babu yarinyar da ke cikin farin ciki a gidansu a gaba dayan kauyen Gurin Gawa kamarta, sabida daurin gindin sangarta da cikakken gata da ta ke samu daga Innarta. "Ke kam 'yar gata ce, Ta-Ummule. Ni uwarki “MAIRO” na tsaya miki. A taba ki a tabo bala'i, A duke ki, in rama miki. Innata ta tsaya min, Ni kuma na tsaya miki........" Sallamar Habibu ce ta katse ta daga wakar da ta ke rerawa 'yar bebinta, cikin zazzakar muryarta kamar gyare. Ta yi cilli da Ta-ummulen ta kwasa da gudu ta makalkale shi, tana cewa, "Yaya Habibu oyoyo!" Ya ce "Ke da Allah kazamar banza, cika ni, dubi bakinki damale-damale da busasshen koko, hanci duk busasshiyar majina, sannan kalli hannunki duk bakin tukunya, kin zo kin goge su duka a jikina. Wallahi duk sanda na doso garin nan cikin fargabar cakumon da zaki yi min da kazantarki nake, shashashar banza an girma ba a san an girma ba". Ya rabata da jikinsa ta karfi, ita ko ko a jikinta, dariya ma ta ke abinta kamar ba da ita yake ba. Inna Hure ta cika fam, kiris ta ke jira ta sauke mishi kwandon bala'in da ke cike taf a bakinta, sabida wannan tijara da yake yiwa autarta. A ganinta Habibu ya tsani Mairo ne kawai, don shi yana birni, ita tana kauye, duk da matsananciyar kaunar da Mairon ke masa. Babu ranar Allah da zata fito ta fadi, Mairo ba ta ambaci sunan Yaya Habibu ba. Shi kuma da zarar ya zo irin tarbar da yake yi mata ke nan, ita kuwa kamar dada tunzura ta yake ta yi masa oyoyon, da dukkan zuciyarta. Ya matsa gaban Innar ya kai gwiwoyinsa kasa, ya ce "Inna barkanku da gida, mun wuni lafiya?" Ba ta juyo daga fifita wutarta ba, haka ba ta kalle shi ba, ta ce "Lafiya kalau". Cikin danne bacin ranta. Ya yi shiru cikin zargin kansa. Ya san tabbas ya tabo Innar, don ta sha ce masa idan ba zai daina kyarar mata auta ba, to ya daina zuwa, babu dole. Cikin kasada ya ce "Amma Inna ga wannan katuwar yarinyar ki zauna kina hura wuta, ita tana wakar 'yar bebi? Duk wani dan arziki kamarta ai yanzu ya dawo ne daga makaranta, yana haramar tafiya islamiyya, amma ban da wannan, ban da karare ba ta san komai ba, shi yasa duk wasu abubuwa na yara masu hankali, ba ta san shi ba............" A fusace ta juyo ta zuba masa jajayen idanunta, ta ce "Kai saurara. Wai me ye gaminka da yarinyar nan ne? Me ta tare maka? In don oyoyon da ta ke yi maka ne ba ka so, zan hanata, amma wannan sababin da kake yi mata ya ishe ni. Ka zo gidan su ka uzzireta babu gaira babu sabar? Ba ta zuwa makarantar, idan kai ka haife ta sai ka dauketa ka kai ta". Ya sunkuyar da kai ya ce, "Allah Ya ba ku hakuri Inna, Inna Allah Ya huci zuciyarku". Ta ja tsaki, "Tsuuuu!" Ta ci gaba da aikinta tana ta sababi, shi kuma bai kara tofawa ba, bai kuma tashi daga durkuson shi ba. Malam Bedi ya yi sallama ya shigo, rataye da fartanyarsa da alama a gajiye ya ke likis, sai gumi ke disa daga wuya da goshinsa. Yana ganin Habibu sai ya fadada far'arsa, amma jin Inna Hure na ta sababi sai ya maida fuskarsa ya dinke. Ya dade yana sauraronta ba ta san ma ya shigo ba, tana ta fadan idan Habibu ba zai daina tsangwamar mata Mairo ba, to ya daina zuwa, don ba ita ta kirawo shi ba. Malam Bedi ya yi gyaran murya, sai a nan tasan da tsayuwarsa. Ta ce "Ai gara da ka zo, dama binka zan yi yanzun, ka ja wa yaron nan kunne ya sakar wa diyata mara ta yi fitsari, tunda ba a gidansu ta ke zaune ba, balle ya ji kunya don an ce kanwarsa ce". Malam Bedi ya ce, "Anya Hure? Kina kyautawa abin da kike yi wa Habibu? Ina laifinsa don ya zo gaishe ki? Wannan yarinya da kike ta tada jijiyar wuya akan an gaya mata gaskiya, wane ne majibincin al'amarin ta nan gaba a bayan mu? Wannan din dai da kike cewa ya fita harkarta shi ne ba wani ba. To idan ya fita harkar tata ranar da babu mu, wane ne zai shiga? Shin ma me ya yi mata da zafi? Don kurum ya ce ta dinga wanka? To ki yi hakuri, Habibu ya daina cewa 'yar ki ta yi wanka, don Allah ta shekara ba ta yi ba. Kai taso mu tafi masallaci kar mu rasa jam'i". Ai jin haka ta yi daki da gudu ta yayibo mayafinta da takalmin robarta, a gujen ta sake fitowa, "Yaya Habibu ni ma zani masallacin, dama tun jiya ban yi sallah ba". Wani takaici ne ya sake kama shi, ya hadiye ya ce, "To mu je, amma sai ki tsaya a wajen masallacin daga gindin bishiya kina bin jam'in, don mata ba sa zuwa masallacin maza". Ta ce "To idan mun fito zaka rakani mu je mu tsinko wa Inna tsamiyar kunu? Dama Rabe shi yake dora ni, kai kuwa ka ma fishi tsawo". Ya kama baki, "Yanzu Mairo bishiyar tsamiya kike hawa?" Cikin son ta burge shi, da alfaharin hakan sosai a kwayar idonta, ta ce "Mu hau tsamiya mu sauko, mu hau magarya, mu hau dinya, mu tsallaka goba. Rannan Lanto ta fado tim! Ta karya kashin baya, ni kuwa idan na makale a jikin reshen bishiya kamar 'yar Birrai nake. Bana fadowa, sai dai in ciko bujena da goba da tsamiya........." Ya yi gaba ya rabu da ita don takaicinta kamar ya amayo zuciyarsa, amma sai ya yi tunanin to ita me ye laifinta? Innarta ce ta daure mata gindi. Habibu saurayi ne dan kimanin shekaru ashirin da biyar. Ya kammala kwalejin horas da malamai ta Kano, wato (SAS), yana jiran sakamako ne ya wuce babbar makaranta, kodayake ma abin da ya kawo shi Gurin-Gawa kenan yanzun, wanda yake son su tattauna da mahaifinsa. Alhaji Abbas Mai goro kanin Malam Bedi ne ciki daya, uwa daya uba daya, shi ke rike da Habibu da hidimar karatunshi, ko da yake morar juna suke tunda kuwa duk wahalar kasuwancinsa na goro, a wuyan Habibun ta ke, wadda ya ke gudanarwa idan ya dawo daga makaranta da ranakun karshen mako. Suna zaune a unguwar Yakasai a cikin birnin Kano. Yana da matan aure biyu da 'ya'ya bila adadin maza da mata. Saidai ‘ya’yanshi kanana ne da ake haifa akan idon Habibu. Cikinsu duka babu mai shekaru goma. Babbar diyarshi Ladidi sa’ar mairo ce. Don haka Habibu tamkar wani jigo ne ga iyalin Alh. Abbas wanda duk suke kauna sabida zumuncinsa da rikon amana. A rayuwar Alh. Abbas bai taba ganin yaro mai kwazon neman na kai da amana irin Habibu ba. Tunda ya ke tare da shi, kwandala wannan bata taba bata cikin lissafinsa ba, kimanin shekaru ashirin ke nan. Watau tun Habibun yana dan shekara biyar. Wannan ne dalilin da ya sa ya maida Habibu dan cikinsa ba Dan dan uwansa ba. Taimako dai-dai gwargwado Alh. Abbas na yi ma yayan shi Malam Bedi, kamar ta samar mai ingantaccen takin zamani, da taimaka mai da motocin noma a yayin girbi, wadanda yake dauko masa haya daga KNARDA. Bayan wannan sallah da azumi shi ne sutturarsu, haka ta fannin abinci lokacin azumi, tun daga kan sukari, lipton, madara, da su taliya ba abin da ba ya taso Habibu ya kawo musu, sai dai idan suna nomansa a nan Gurin-Gawa. Zumunci ne mai karfi a tsakaninsu, wanda iyayensu suka dora su a kai, har gida Alh. Abbas ya sayawa Mal. Bedi a Yakasai ya ce ya dawo su zauna tare, inda shi kuma ya ce shi da rabuwa da Gurin-Gawa sai dai mutuwarsa. Ko ita ba ya fatan a fitar da gawarsa daga Gurin-Gawa, su je can su tsinci abin da suke tsinta a birnin, shi kam a gareshi kwanciyar hankali shi ne komai. To amma wannan zumunci na mazan ne banda matan. Babu shiri ko kadan tsakanin Inna Hure da matan Alh. Abbas wato Habiba da Hajara. Tun sanda daya daga cikinsu ta taba cewa a bata Mairo ta dinga taimaka mata hidimar ‘ya’yanta ta kulla gaba da su. Ta ce kuma wadda duk ta kara tako mata gida, Allah Ya isa. Ta rasa dalilin da 'yar tata ta tsolewa kowa ido. Ba abin da ta ke so a rayuwarta irin ta budi ido ta ga Mairo na wasan 'yar tsanarta a tsakar gida, suna harkokinsu gwanin ban sha'awa. Don haka ne ko makarantar firamare da ake sa yara a kauyen taki yarda ta sakata, ita dai su zauna abinsu. Sai da Mal. Bedi ya yi da gaske kamin Mairo ta dinga zuwa karatun allo a makwabtansu, daga takwas na safe zuwa sha biyun rana. Nan din ma ba wani abin arziki ta ke tabukawa ba da ya wuce tsokana, jan fada, surutu da guduwa idan Malam ya soma gyangyadi. Abin da Mairon Hure ta kware akai shi ne hawa bishiya. Yadda kasan kadangaruwa koko Gorilla haka ta ke makalewa a jikin bishiya. kusufa-kusufa ta iya kurdawa ta tsinko abinda ranta ke so ta cika bujenta. Duk girman bishiya Mairo zata iya dafe ta, ko tsoron irin aljannun nan da ake ce suna zama a bishiyoyi ba ta yi. Ta tsinko musu su ci abinsu, ita da Innarta, wannan ya fi komai dadi ga Hure. Mairo yarinya ce 'yar kimanin shekaru takwas cif. Amma kaifin bakinta ya fi na dan shekaru ashirin. Kyau kam ba a magana, tsurarshi na Inna Hure, doguwa shafal-shafal da shafaffar mara gami da lafiyayyen kugu, wanda tun tana jaririya haka yake. Sumar kai yalwatacciya, yalo-yalo kamar ta hada jinsi da Larabawa. Sai dai fa dankare take da kwarkwata da amosani wanda ya bi ya cinye rabin gashin. Wani aiki sai Hure Innar Mairo, don tunda Mairo kukan kitso ta ke, aka shafe yi mata kitso a doron kasa. Kai wata kila ma ta manta akwai suma akan Mairo, don kullum kulle ta ke tamau cikin wani bakin dankwali mai masifar dauda. Sai idan kwarkwatar ta ishe ta da cizo ne ta ke tube dankwalin ta samu gefe guda ta yi ta susa da hannu bibbiyu har sai jini ya bubbugo. Wannan shi ne babban takaicin rayuwar Habibu, yana matukar bakin-ciki da tsarin rayuwar kanwarsa tilo, wadda kuma Allah Ya sanya masa matsananciyar kaunarta da tausayinta. Ta wani bangaren ba ya ganin laifin Inna Hure, domin haihuwar ce Allah Ya ba ta a tsufanta, bayan ta riga ta fidda rai da samunta. Sannan yawan aiyukan gida da ke kanta ba zasu barta ta kula da irin wadannan kananun abubuwan game da yarinyar ba. Duk ba wannan ya fi damunsa ba, kamar jahilcin Mairo. A ganinsa Mairo jahila za a kirata kai tsaye, ba arabi ba boko. A ganinsa da tana zuwa makaranta, wannan duk wani abu ne da ita kanta zata yi wa kanta nan gaba, ba tare da kowa ya sata ba. Bayan sun fito masallacin ya duba inda ya ce Mairo ta tsaya ta yi sallah, ba ta ba alamunta, balle dardumar karauninta. Ya juya gabas da yamma, Kudu da Arewa babu Mairo. Ransa ya sosu, ya kira wata 'yar yarinya mai tallan rogo, ya ce "Don Allah ko kinga Mairon Hure?" Ta ce, "Na ganta ta mika kwanar gidan su". Ya ce, "To madallah. Ta yi gaba abunta dai-dai sanda Malam Bedi ya cimmasa da cazbaha a hannunsa ya ce, "Mai kake tambaya ne?" Ya ce "Mairo mana, sama ko kasa na nemeta na rasa?" Dariya ya ba wa Malam Bedi, ya ce "Mairon ce zata zauna maka waje daya? Ai yadda kasan tsuntsuwa haka ta ke. Idan dai ba gaban Innarta ba ne babu inda zata zauna. Ai jin ku kawai nakeyi da ka ce wai ta zauna nan mu fito". Ya girgiza kai suka ci gaba da tafiya yana ba shi labarin Mairo. Wanda duk mai bakanta zuciya ne ga Habibu. Ya ce "A rana in ba a kawo min kararta sau hudu ba, a kawo sau shida. Malaminsu ya gaji da sulalewar da ta ke yi, ya ce ta yi zamanta gida. Ni al'amarin Mairo ai sai addu'a. Kuma duk Hure ce ta jawo". Habibu ya yi kankan da murya ya ce "A gaskiya Baba kai ma da naka laifin. Mai yasa idan Innar ta yi hukunci akan Mairon ba ka ketarewa? Yanzu sabida Allah kamar Mairo ace har yanzu ba ta shiga makarantar boko ba, sai yaushe? Sai karatun ya wuce lokacinta? Fisabilillahi ina matukar takaicin rayuwar Mairo. Ina tausaya mata, domin dai ita 'ya mace ce, gidan wasu zata je ba da jimawa ba. Babu mijin da zai iya zama da ita da wannan rashin tarbiyyar wadda ni ba haka aka yi mun ba". Ya yi shiru kamar zai yi kuka, zuciyarshi na matukar kuna. Malam Bedi da alama zancen Habibu na shigarsa. Ya ce "Yanzu ni me zan iya akai Habibu? Ba karamin abu ba ne Hure ta amince akai Mairo makarantar book ba. Ni kuma bana son tashin hankali balle abin da zaya bata mini rai, ina zamana lafiya". Habibu ya dubi mahaifinsa cikin ido, ya ce "Shin Baba kai ko Inna wa ke auren wani?" Malam Bedi ya ce "Ni ne". Ya ce "To matukar kai ke da iko da ita dole ka ba ta umarni. Kuma dole ta bi idan dai ita matar kwarai ce. Ka daina tsoron sababinta, kai ma ka bude mata murya. Ita ma ta iya ta bude maka makogwaro balle kai?" Ya yi murmushi ya ce "To yanzu me za a yi?" Ya ce, "Ni zan je na samu hukumar makarantar in musu bayani har halayenta duka zan fada musu, don su yi hakuri da ita, su kuma san matakin da za su dauka a kanta idan ta gudo ba tare da sun yi la'akari da fadan Inna ba. Ga kuma makarantar islamiyya da na ga yara suna zuwa da hijabinsu da uniform, nan ma zan je in ba da sunanta su sanyata ajin da ya dace da ita. Kai kuma aikinka shi ne ka tabbatar tana zuwa akan lokacin, da son ranta da na Innar ko babu?" "Malam Bedi ya ce "Sha Allahu za a yi kokari. Allah dai Ya yi maka albarka Habibu, idan ban da kai dan uwanta wa ya damu da ita balle har ya ce a sanyata makarantar?" Habibu ya ce "Sai abin da ya kawo ni, amma ina ganin mu samu gindin bishiyar can mu zauna, maganar ta zaune ce". Malam Bedi ya ce "Inji dai ALHERI ne?" Ya ce "Alheri ne, idan Allah Ya so Ya yarda, kai ma ka yarda". Suka samu kututturen bishiyar wata goriba mai duhu da inuwa mai sanyi suka zauna. Malam Bedi ya tattara dukkan hankalinsa akan Habibu, yana zake da son jin mai zai fito daga bakinsa. Shi kuwa Habibun in banda addu'ar neman rinjaye babu abin da yake dannawa Malam din daga zuciyarsa. Malam Bedi ya ce "Kai na ke saurare, kuma ka yi shiru". Habibu ya ce "Eh to, dama Alhaji ne ya ce in zo in shawarce ka, ko kuwa in nemi izninka, idan ka yarda shi ke nan. Idan ma ba ka yarda ba babu damuwa sai na hakura". Ya ce (a dan kufule) "Wai mene ne ka ke ta kwana-kwana? Daga ji ba abin arziki ba ne, don abu idan na arziki ne ba a kumbiya-kumbiyar fadarsa". Ya yi murmushi ya ce "Yi hakuri Baba. Wani abu ne na zamani ya shigo mana cikin na'ura mai kwakwalwa wai shi yanar-gizo (internet). Ta cikinshi babu inda ba zaka sadu da shi ba a duniya. To rannan ina lalube na, sai na ci karo da tallan wata makaranta a Malaysia suna neman dalibai. Kamar da wasa na cike form dinsu na tura musu. To kwatsam har na manta, shekaran jiya sai ga sako sun turo cewar sun dauke ni, na zo na biya kudin makaranta na fara karatu. Na samu Alhaji na fada masa, ya tayani murna kwarai, to amma shi kansa ba ya da kudin da zai iya daukar nauyin karatun, amma yace zai yi min hanyar da zan mika neman taimako daga gwamnati ta hanyar wani abokinshi mai baiwa gwamna shawara akan harkokin matasa wai shi ALHAJI GAMBO ADO, kuma ya tabbatar min za a samu insha Allahu, ragowar shi Alhajin ya yi alkawarin cikasawa daga aljihunshi. Shi ne ya ce na zo na fada maka tun kamin komi ya yi nisa, kada sai an gama wahala ka zo ka ce ba ka yarda ba. Yanzu kuwa ba abin da aka yi, sai da amincewarka". Shiru Malam Bedi ya yi kamar ruwa ya cinye shi, yayinda Habibu ya ci gaba da jifansa da, "Innahu ala raja'ihi la-kadir". Bai gushe ba yana maimaita addu'arsa sai jin muryar malam Bedi ya yi tana tambayarsa har tsayin shekaru ko watanni nawa za a yi ana karatun? Ya yi godiya ga Allah a zuciyarsa, domin da alama akwai nasara, ya ce "Abin ya fi karfin watanni. Shekaru shidda ne zan yi ina karatu akan na'ura mai kwakwalwa". Malam bedi ya ce "To daga nan kuma fa?" Habibu ya murmusa ya ce "Sai na dawo gida na nemi aiki". Malam Bedi ya ce "A'ah, ba haka nake son ji ba, sai ka dawo ka yi aure ka tara min 'ya'yan da ni Allah bai bani da yawa ba". Habibu ya sunkuyar da kai yana murmushi, ya ce "Insha Allahu Baba". Malam Bedi ya ce "To ka je, Allah Ya tabbatar da ALHERI……....." Dai-dai nan Habibu ya ji “tim!” A tsakiyar kansa an nannako masa katuwar goriba a tsakar ka. Kwakwalwarsa ta daure, kansa ya yi dumm!! Kamar an kwala masa dutse. Wata azaba ta ziyarce shi tun daga tsakiyar kansa har yatsar kafarsa. Kamin ya gama farfadowa daga takaitaccen suman da ya yi, sai jiyo zazzakar muryarta yayi kamar zata tsige masa dodon kunnuwa tana fadin "Yaya Habibu sanya min a aljihunka, nawa aljihun bujen ya cika……..". Suka daga kai su duka biyun suna kallonta, Mairo ce kwance abinta akan reshen bishiya, a kalla ta fi karfin awanni biyu akan bishiyar. Tunda liman ya tada kabbarar sallah ta yi raka'a daya ta dago, ta hango goshin kowa a kasa, babu mai kallonta, ta yayibo tabarmarta da zummar tahowa gida. Sai kuma ta hango nunannun goriba ai kuwa ta daka tsalle ta dare. Duk abin da suke cewa akan kunnenta, sai dai ba wani fahimta ta ke yi ba sabida hankalinta ba ya jikinta. Ita dai tana tsinkar goribar ta gutsira ta ji idan da zaki ta sa a buje, idan ba zaki ta cillar. Sai da bujen ya cika ne ga shi kuma ba ta iya barin wannan zazzakar, ta cillowa Habibu ajiya. Ya bude baki da kyar ya ce "To sauko mu tafi". Ta ce "Bari na tsinkowa Baba". Ya ce "A'ah, shi baya da karkon hakori". Ta kamo reshe bayan reshe tana bin jikin bishiyar cikin kwarewa har ta sauko suka taho gida. A ranar da ciwon kai ya kwana, amma bai daina yi wa malam Bedi magiya da naci akan makarantar Mairo ba, ko baya nan. Malam din ya yi masa alkawarin kada ya damu, da yardar Allah kamin ya dawo Mairo ta kimtsu. Washegari ya je ya ba da sunanta a makaranta aka sata aji uku. Ya yi musu bayaninta dalla-dalla wani malami da yake makocinsu ne ya ce ya san Mairo farin sani, ko shi yana takaicin rashin sa ta makaranta, to amma kowa ya san sababin Inna Hure, idan dai akan Mairo ne, shi yasa kowa ya sa mata ido. Amma insha Allah zai tsaya a kanta kamar yadda zai tsayawa 'yar cikinsa. Habibu ya yi godiya mai tarin yawa, ya nemi taimakonshi a kan ya taimaka ya bayar a dinka mata uniform, ya kirgo kudi ya ba shi har na littattafai da jakar makaranta. Sannan ya nufi islamiyyar yaran Gurin-Gawa, nan ma ya ba da sunanta. Sun tabbatar mishi ba komai ai irin su Mairon ake son a gyara. Hankalinsa bai kwanta ba, sai da ya ga Mairo ranar litinin cikin kayan makaranta da jakarta a rataye ta tafi makaranta. Duk da Inna Hure na kumbure da shi, bai damu ba, tunda ya cika kudurin da ya dade yana damun zuciyarsa. Don haka koda ya je yi mata sallama zai komo Kano ta yi masa kunnen uwar shegu. Hure ta ga tijarar Malam Bedi irin wadda ba ta taba gani ba, ba ta kuma taba tsammanin ya iya ba, domin cewa ya yi idan Mairo ba zata je makaranta safe da yamma ba, to dukkaninsu su zo su fice masa a gida, su tafi duk duniyar da za su. Ba ta yi magana ba, amma a cikin ranta tasan wannan aikin Habibu ne, don yadda Malam din ke jin maganar Habibu ko ubansa sai haka. Abin da ta ce da shi kawai shi ne, "Saboda ka tabbata tsohon bakauye ka zauna dan ka ya fi karfin ka". Ya ce "Eh, koma mai zaki ce ki ce, amma Mairo da uwarta ba su zama min cikin gida muddin Mairo ba zata nemo ilimi ba. Me ye marabarta da dabba? Babu! Dabba ce aka sani da hawa bishiya da cin abincinta daga 'ya'yan itace, amma ba dan mutum ba". Habibu ya karkace kai ya yi ta ba Innarshi hakuri, ya ce "Inna ku yarda da ni, ba ni da nufin cutarku, sai dai ma na yi kokarin ganin duk abin da zai zamto cuta a gare ku na yake shi iya karfina. Ina nufin Maironki da alheri ne, bayan wannan ba wani abu. Ke da kanki wata rana za ki gane gata na yiwa rayuwar Maryam. Don Allah Inna ki sauko ki yafe min, kisa min albarka!". Zuciyarta ta yi sanyi lakwas, ta ce "Ai shi ke nan, nasan iyakar gaskiyar ke nan, laifina shi ne, ina son Mairo da yawa". Ya yi murmushi ya ce "Hakan ma ba laifi ba ne. Sai dai ki yi kokari kada son da kike mata ya sa ki kasa lankwasata. Ni ma ina son Mairon ki, son da bana yi wa kowa a duniya, amma idan har da gaske ina sonta, dole in inganta mata rayuwa da gishirin zamani, wanda idan babu shi miya duk dadinta lami ce. Wannan gishirin kuwa ba komi ba ne, face wannan ilimin dana ke so Mairo tayi. Shi ne zai haskaka mata ragowar bangarorin rayuwarta, tasan kanta, tasan inda ta sa gaba. Amma a yanzu wallahi Mairo ba ta da maraba da 'ya'yan birrai". 7/28/21, 10:59 AM - Buhainat😝: 80 Dariya Inna ta yi, ta ce "To Allah Ya taimake mu ta kimtsu". Ya ce, "Amin--amin, ko ke fa Innata? Ni ma karatun zan tafi..." Ya warware mata zare da abawa. Ga mamakinsa sai ya ga damuwa karara ta bayyana a kyakkyawar fuskarta, ita da a kullum, ta ke nuna ba ta damu da shi ba. Ya shiga kwantar mata da hankali cikin tausasan kalami, yana nuna mata shekaru shida kamar yau ne, idan da rai da lafiya. Da kyar ya samu ta sa ma abin albarka. Da wannan Habibu ya koma Kano ya ci gaba da shirye-shiryensa, da taimakon Baffansa. Cikin watanni uku kacal komi ya kammala, ya zo wa iyayenshi sallama. Ya ji dadin yadda ya ga Mairo cikin wankanta fes! Ba ta kuma yi masa wannan damuken oyoyon ba, an fara nutsuwa ke nan. Ya yi murmushi, ya ce, "Mairon Inna 'yan makaranta, ya ya dai?" Ta yi murmushi ta kawar da kai ba ta ce komi ba. Ya kamo hannayenta ya ce "Ba ki ga yadda kika soma sauyawa ba? Ina fatan duk runtsi za ki dage da zuwa makaranta? Zan tafi karatu Mairo, sai Allah Ya dawo da ni kimanin shekaru shidda a nan gaba. Ki kula da Innarki, ki dinga tayata aiki, ba wasan 'yar bebi ba kin ji Mairo nah?" Ta shiga damuwa sosai, nan da nan sai ga hawaye rau-rau a idanunta. Ta ce "Yanzu Yaya Habibu shekaru shidda zan yi ban ganka ba? Ina zaka je? Mai yasa ba zaka ci gaba da zama gidan Baba Abbas ba kana zuwa makarantar a can?" Ya ce "Kamar yau ne Mairo za ki ga na je na dawo, idan dai da rai da lafiya. Ki kula da kanki, ki dinga wanka kullum, ki dinga yanke akaifarki ta kafa da hannu duk sati. Ki kuma dinga wanke gashin kanki shi ma duk sati, kin ji?" Ta ce, "Na ji Yaya Habibu, Allah Ya dawo da kai lafiya". Ya ji dadi sosai, bai zaci Mairo tana da dan hankali ba ko yaya ne, har ta yi wa mutum addu'a. Ya sa hannu a aljihunsa ya ciro naira ashirin ya bata, ta yi ta murna ta je tana nunawa Innarta. Haka Habibu ya tafi cike da tunanin Mairo. Yana addu'a, Allah Ya sa ta dore da hakan. Watau turbar da ya sanyata. Washegari ya tashi zuwa Malaysia, inda ya samu gurbi a Unibersity of Malaya. Ya sha wuya matuka kamin ya samu ya mance da tunanin gida. Da taimakon abokinshi Amiru wanda shi ma dan Kano ne ya samu ya soma fuskantar karatun, amma babu ranar Allah da zata fito ta fadi bai tuna Mairo ba. *** BAYAN TAFIYAR HABIBU M alam Bedi tsaye yake akan kafafunshi kan karatun Mairo don cika alkawarin da ya daukarwa Habibu. Da taimakon Allah Mairo ta saba da zuwa makaranta, kuma lokuttan makarantar sai ya shafe lokacin da ta ke samu ta hau bishiya ko ta yi wasan 'yar tsana. Idan ta dawo makaranta karfe daya na rana wanka zata yi ta ci abinci, ta yi sallah. Karfe biyu cikin ajinsu na islamiyya ya ke mata. Ba kuma za su taso ba sai goshin magriba, don haka ranakun alhamis da juma'a da yamma kadai ta ke samun hutu. A cikinsu kuma tana tare da Innarta suna ayyukan gida wadanda ta alkawarta wa Yaya Habibu taimakawa Innar. Rannan Mairo na surfen masara Inna Hure tana bakacewa, Mairo ta aje tabaryar ta ce "Oh Inna, Yaya Habibu yau watanninsa bakwai ke nan, yana can a cikin Turawa". Inna ta ce "Wa ya ce miki a Turai yake? Kasar Larabawa ne". Mairo ta yi murmushi, ta ce "A'ah Inna, rannan na tambayi malaminmu na makarantar book, a ina Malaysia ta ke? Ya ce min Asia ne, can wajejen India da Pakistan". Inna ta kama baki ta ce "Ke Mairo, yaushe kika iya Turanci haka?" Mairo ta ce "Ba Turanci na yi miki ba Inna, sunan kasashe na fada miki". Wani dadi ya kama Inna Hure, ba tasan sanda ta ce "Kai Allah Ka sakawa Habibu da alheri” MARYAM BEDI, ta ci gaba da karatunta cike da himma da kwazo. Takan sanya wa ranta cewa, kawai Habibu na kallonta, yana jin dadin kwazonta. Yana kara mata karfin gwiwa. Ba ta yarda wai shekaru shidda zai yi bai dawo ba. A ganinta shi ne Habibu na iya dawowa yau, ko gobe, don kawai ya rutsa ta, ya ga irin kwazonta. Saboda haka cikin shekara guda kacal, Maryam Bedi, ta zama zarrah a ajinsu na boko, kan gaba a ajin islamiyyah, wadda ke da haddar izfi ashirin na Alkur'ani a cikin kanta. Sauran littattafan addini kuwa idan ta bude su tana karantawa tana fassarawa Inna tsarki da alwala, da irin sallar khashi'ai da sallar da ake dunkulewa a jefowa bawa kayarsa, tun kamin ya tashi akan dardumarsa. Sai Inna ta sa habar zaninta tana share hawaye, ta ce "Ba karamar cuta na so na yi miki ba Mairo". Shekaru uku ke nan cif da tafiyar Habibu, kuma a yau ne ranar saukar su Mairo. Ta sha wanka da sabon dinki na atamfa (hitarget) da suka yi anko gaba dayansu. Ta dora wani sabon farin hijabi akai, wanda ya tabo har gwiwarta. Ta azalzali Innarta ta yi sauri ta gama shiryawa su tafi kada wajen zama ya cika ta rasa inda za ta zaunar da ita. Innar kuwa sai sake murza kwalli ta ke a idanunta yadda zata fito radau! Ta kuwa fito din, sai kyallin wanka da basilin ta ke. Suka jera abinsu Mairo na ta addu'ar samun nutsuwa cikin zuciyarta sakamakon ganin cincirodon al'ummar kauyensu wadanda ake nufin ta yi karatu a gabansu. Tuni Malam Bedi ya isa wajen tun kamin su zo, yana cikin rumfar iyaye maza, a sahun gaba, yana ta ware ido don ganin ta inda Mairo zata bullo. Can ya hangota rike da hannun Innarta, ta samu wajen zaman da ya dace da Innar ta zaunar da ita, sannan ta karasa cikin 'yan group dinsu suka yi sansani. Taro ya yi taro, mai gabatarwa ya fara gabatarwa bayan bude taron da addu'a, daga limamin garin Gurin-Gawa. Maryam Bedi, ita ce wadda aka fara kira ta bude taron da karatun Alkur'ani cikin daddadar kira'arta kai ka ce diya ce ga Khusairi, inda ta karanto karshen suratul Fathi, wato ayar nan ta "Muhammadurrasulullah…...." Gaba dayan jama'ar dake wajen jikinsu ya yi sanyi, sai ga Malam Bedi yana kuka. Da ta dasa aya aka dauki kabbara kowa na cewa "Ai Mairon Hure ce, diyar Malam Bedi". Innar kuwa sai washe baki ta ke, bakinta ya ki rufuwa don kuwa duk matan da suka san ita ce babar Mairo, sai gaisawa suke da ita. Yayin da 'yan bakin-ciki, wato wadanda ke da 'ya'ya a makarantar ba a kuma kirawo 'ya'yansu ba sai zumbure-zumbure suke yi mata, ko a jikinta wai an tsikari kakkausa. Haka nan Mairo ce dalibar da aka fara kira ta amshi allonta daga hannun Mai girma shugaban karamar hukumar Kumbotso. Malaminsu ya karanto mata farkon suratul Bakara tana bi tiryan-tiryan cikin kira'ar da ta fi ta malamin. Bayan nan Mairo ta karbi kyautar dalibar da ta fi kowa iya Tajwidi, sannan daliba mafi da'a a gaba dayan daliban shekararsu. A sa'ilin da maigirma Chairman ya amshi lasifika domin gabatar da jawabinsa na babban bako mai jawabi. Budar bakinsa sai cewa ya yi "Na dauki nauyin karatun wannan yarinya MARYAM BEDI a makarantar sakandiren 'yammata ta gwamnatin tarayyah da ke Minjibir". Gabadaya aka sa kabbara. Abokan Malam Bedi suka shiga taya shi murna, ya rasa inda zai sa kansa don farin ciki. Mairo ta riga su komawa gida domin an ce su tsaya za su gana da Chairman. Inna Hure na shigowa ta suri Mairo ta goya a baya, ta sa zane ta daure ta, ta sa majanyi ta kara daurewa. Ta shiga zagaye dakin da ita, ita kuwa sai dariya ta ke. Kamin su zauna gabadayansu. Malam Bedi ya gabatar musu da bayanin da maigirma chairman ya yi masa na cewa, zai tallafawa karatun Mairo a babbar makaranta ta gwamnatin tarayya. Zai mika komai ta hannun shugaban makarantarsu ta boko tunda dama gab ta ke da zana jarrabawar fita firamare. Ya kare da cewa. "Amma fa makarantar ta kwana ce". Nan da nan farin cikin da ke makale a fuskar Inna Hure ya yaye, Mairo ta lura da hakan, ta ce "Haba Inna, wannan ba wani abu ba ne. Zan dinga zuwa hutu kuma ana zuwa ziyara. Kin san Lanto ma ta gidan Kado tana makarantar kwana a Kwa. Duk bayan watanni uku dawowa ta ke. Sannan bayan kowanne wata ana zuwa ziyara". Inna ta ce "To ni wa zai kai ni birni? Har in gano ki a kowanne wata?" Ta ce "Allah Shi zai kai ki, ga iyalin Baba Abbas za su iya raka ki". Nan da nan Hure ta yi kicin-kicin da fuska ta ce "Ke, raba ni da wadannan mutanen. Ni dai na yi hakuri har ki zo hutun". Mairo ta yi murmushi ta ce "Shi ke nan Inna". Malam dai jinsu yake a zuciyarshi yana mamakin dalilin Hure na kin son yin zumunci da iyalin dan uwansa. Bai sani ba ita a ra'ayinta shi ne, idan har zata ke shiga shirginsu wata rana za su sake yin yunkurin rabata da Maironta don taje tayi masu bauta amma ba don Allah ba. Kwanci tashi ba wuya a gurin Allah, su Mairo aka kammala zana common entrace, aka zauna gida zaman jiran sakamako. Ba jimawa ya fito, shugaban makarantarsu ya mikawa Chairman. Cikin sati uku sai ga takardar daukar Maryam Bedi, cikin sabbin daliban FGGC Minjibir na shekarar. A na so kuma ta isa makaranta cikin sati biyu, hedimasta ya kira Malam Bedi ya damka masa ya kuma gaya masa ya hadawa Mairo kayan abinci da ake hadawa dan makarantar kwana, ya kuma ba shi katifar Mairo da filo, domin makarantar ba sa bukatar akwatun karfe. Malam Bedi ya dawo gida shi da Hure aka hau shawarar abin da za a hadawa Mairo, Hure ta daka mata kuli-kuli ta kuma shanya mata Rama mai yawan gaske, da zata dinga jikawa idan ta yi sha'awa ta kwada ta ci, kwaki kwano biyar, kanzo kwano uku, yaji rabin kwano, omon wanki da sabulun wanka. Man shafawa da man kitso, man kuli da manja. Mairo ta ce, su sayo mata brush da maclean, aka siyo a Fanshekara. Shi ke nan kaya sun hadu sai tafiya. A daren Inna Hure ta kwaba lalle ta yaba mata a kafafunta aka daure aka kuma zura hannun dama cikin dumar lalle, shi ma kan safe ya yi jawur kamar jini, duk adon tafiya makaranta ne. Aka tsefe kai aka yi mata kitson doka guda takwas. Babanta da Hedimasta su za su kai ta Minjibir, don haka tun karfe bakwai hedimasta ya ke buga musu zaure da yake shi ma Chairman ya cika shi da abin arziki duk don ya kula da karatun Mairo. Mairo na kuka Innarta na yi, a haka suka rabu. Hedimasta dauke da katifar kwanan Mairo, malam Bedi rike da dindimemiyar (Ghana Must Go), a haka suka doshi tasha. Hedimasta na ce da Bedi daga wannan zuwan da zamu yi da kai, duk hutu kai kadai zaka dinga kawota, don haka ka dinga kula da duk abin da na yi". Malam Bedi ya ce "To, angode dai". Suka samu bayan motar rake suka dane, ta fito da su Fanshekara, daga nan suka hawo motar Bata/Kuroda. A nan suka hau motar Minjibir, Mairo a maleji su kuma a kujerun gaban motar. Tafiyar awanni biyu ta kawo su Minjibir, aka sauke su a tasha. Daga nan suka hau tasi aka kai su har kofar FGGC. Suka gaisa da maigadi, suka ba shi ajiyar kayan su suka karasa cikin makarantar. Jikin Mairo ya yi sanyi matuka ganin irin tsaleliyar makarantar da aka kawo ta. Ta daga ido tana hangen dalibai cikin kayan makaranta iri daya, cikin tsari da nutsuwa. Kowacce a nutsenta ta ke tsaf, tana tafe cikin kamala. Ba ka jin hayaniyar komi sai sautin malamai suna koyarwa cikin azuzuwa, shi ma din a tausashe. Mairo ta kalli kanta sama zuwa kasa, ta hango bambanci a farrake tsakaninta da irin jefi-jefin daliban da ta ke ganin suna wulgawa. Gabadaya sai ta ga kanta kamar wata almajira, duk da kuwa ta kure adaka, ta sha lalle. Ga jambaki jawur ta rambada ta yi kuma jagira da digo a tsakiyar goshinta. Duk da hakan ba ta ji ko dar na zama a wannan makarantar ta yi karatu ba. Ta yi tunanin cewa, ba wannan ne abinda ya kawota ba, darasin da za a koya mata ne, Yaya Habibu ya dawo ya yi alfahari da ita. Suka tambayi ofishin shugaba aka nuna musu. Kai tsaye can suka dosa, Mairo na kallon yadda daliban wani aji da babu malami a ciki suka yi cincirodo a taga suna kallonta. Sai hankalinta ya tashi matuka, don haka har ta riga Hedimasta tura kai ofishin shugaba, don dai ta tsira daga kallon wadannan yara. Shugaban makarantar Halima Dukku, ta yi tsai da ranta ta cikin gilashinta tana kallon harbatsatstsiyar dalibar da aka kawo mata. Ta jinjina kai ba tare da ta tofa ba, ta karbi takardun hannun Hedimasta ta sa hannu bayan ta duba ta kuma shigar da sunan Maryam Bedi cikin jerin daliban da makarantar ta karba a wannan shekarar. Ta sa aka ba ta uniform, house-wear da sauransu. Ta kalli takalmin da ke kafar Mairo ta ga silifa ne, wani bakikkirin da shi, ya kuma hadu da wata kafa jawur kamar gauta. Ta ce ba sa ba da takalmi don haka aje a sayo mata sandal ko cambus. Hedimasta ya ce su yi masa alfarma ya bada kudin a siya mata, su baki ne a garin ba su san ko ina ba. Ta kira leburanta, ta hadasu dashi, ya gaya masa sandal dari takwas ne, kambas dubu daya da dari biyar mai saukin kudin kenan. Gabadayan su shi da Malam Bedi suka hada baki suka ce, "Mai ka ce?" Ya sake maimaitawa. Malam Bedi ya hau salati amma shi Hedimasta da yake da dan karatunsa na yaki da jahilci sai ya ce"Au to, ba mu sani ba ne, domin yanzu a aljihuna kwata-kwata naira dari hudu ne, ga shi a ciki zamu hau mota. Amma ga wannan". Ya mika masa dari biyu, ya ce, "Ko irin na dankon nan ne mai igiya a saya mata idan zata dawo sai a nemo". Haushi ya ishi leburan ya juya zai fita abinsa, shugaba ta yi gyaran murya ta dauko gudar naira dari biyar guda hudu ta mika masa, ba tare da ta ce komi ba. Malam Bedi ya dinga zuba mata godiya, ta ce, "Babu komi, ai da na kowa ne". Ta sa aka kira mata wata prefect ta hadata da Mairo da kayanta gami da littattafai wadanda suke cikin kudin makarantarta, amma babu jaka, ta ce su sayo mata daga baya, ta ce ta kai ta hostel. Sai a lokacin ne kuka ya zo wa Mairo, shi ma Malam Bedi duk da dauriyarsa sai da ya sa habar babbar rigarsa yana share hawaye. Suna dagawa juna hannu har su Mairo suka kule cikin hostel. Bayan prefect din nan ta damka Mairo a hannun house-captain dinsu sai ta koma aji. House-captain ta nunawa Mairo dakinsu ta ba ta gado ta shimfida katifarta ta ce, to ta sanya uniform ta tafi aji don kowa yana aji. Sai dai fa a ranta tana mamakin yadda aka yi wannan bakauya ta zo makarantarsu. Mairo ta tube kayanta ta sanya na makaranta ta bi bayan captain har ajin da aka ba ta, wato JSS 1A. Ta je staff room ta nemo class master dinsu ta hada shi da Mairo, ta koma nasu ajin. Mairo ta yi tsuru a gaban allo, a lokacin da Uncle ke gabatar da ita a matsayin sabuwar daliba a ajin. Abin da Mairo ta lura da shi shine, gabadaya 'yan ajin wani irin kallo suke mata na raini da kyama, suna kyabe baki duk sai ta ji ta muzanta. Uncle ya nuna mata kujerar zama gefen wasu fararen yara 'yan gayu guda biyu, da ba su fice tsaranta ba. Ai kuwa suka soma matsawa jikin junansu suka takure suka ba ta katon fili. Malamin ya lura da irin karbar da Mairo ta samu a ajinsa, duk sai ya ji tausayinta ya kama shi. Ya dube ta ya ce, "Sake gaya min sunanki, ban gane abin da principal ta rubuta sosai ba". A hankali ta bude dan kankanin bakinta ta ce "Maryam Bedi". Ya ce "What a nice name, maryama, saki jikinki ki zauna a inda na umarce ki. Ba ruwanki da kowa sai abin da ya kawo ki, kina ji na?" Ta gyada kai, amma ba ta amsa ba. Ta karasa inda ya nuna mata ta zauna a darare. Yarinyar kusa da ita ta ja tsaki, tsuuu! Ta murguda baki ta juya mata keya. Ta dauki tulin littattafanta ta zura su cikin lokar kujerarta tunda ba ta da jaka. Uncle ya fita cike da tunanin wannan yarinya. Yana daga cikin malaman da ba sa son ganin rashin walwala ko yaya daga dalibansu. Abin da ya lura shi ne, Maryama ta shigo makarantar da ta fi karfinta. Ya fi kowa sanin girman kai da ji da kai na daliban FGGC don haka ya samu kansa da tausayin 'yar yarinya, Maryama. Ya alkawarta wa ransa taimaka mata iyakar iyawarsa, har sai ya ga ta saki jikinta tamkar sauran dalibai ‘yan uwanta. Da aka tashi daga aji Mairo ba ta san dawar garin ba. Ta dai ga kowa na fita da littattafansa babu wanda ya kulata, kai ba ta ma ishi kowa a ajin kallo ba. Sai ta kwaikwayi yadda suka yi, wato ta kwaso littattafanta masu yawa da matukar nauyi ta nufi hostel kamar yadda ta ga sun yi. Tana shiga dakin sai ta ga wadannan fararen yaran sun rigata isa har sun tube uniform sun sa na hostel, ashe su ma a dakin suke. Suna ganinta ta shigo suka kara yin kicin-kicin da fuska kamar an aiko musu da sakon mutuwa, musamman da suka fahimci a kusa da gadonsu ta ke. Dayar ta yi tsaki ta canza harshe tana cewa da kawarta, "See this girl, i donno what she is looking for here..."(kalli wannan yarinyar bansan me take nema a nan ba). Kawar ta ce, "Kaddararmu ke nan, daki daya, aji daya, mts!" Jikin Mairo ya kara yin la'asar, amma sai ta dasa wa ranta ta rabu da wadannan yaran ta yi abin da ya kawo ta. Ta ajiye litattafanta ita ma ta tube uniform tasa na hostel irin wanda taga sun sanya, ta nufi famfunan da ta ga ana alwala, ita ma ta yi ta nufi masallacin da ta ga ana shiga da sauri ta samu jam'in sallar azahar. Da aka fito yunwa ta addabe ta, ta soma tunanin ta je ta kwada kwadon kwaki sai ta ji wata senior na fadin a fita ‘dining’ za’a rufe hostel. Ta dinga maimaita kalmar 'dining' a ranta, ko mene ne? Ta ga dai kowa fita yake yi sai ta bi bayan wasu yara ba tare da sun san binsu ta ke ba, har zuwa wani katon dakin cin abinci inda ta ga dalibai a zazzaune kowa da filet dinshi ana ta cin abinci. Yawun bakinta ya tsinke, ta bi layin da ake bi a karba ita ma ta karba, jallof din shinkafa ce da yankan nama biyu da soyayyar ayaba (plaintain) sala uku. Ta zauna ta ci ta koshi, ta sha ruwa ta yi hamdala ta mike ita ma ta nufi hostel ta kwanta a gadonta don ta huta zuwa la'asar. Da aka yi sallar la'asar kuma suka koma aji zuwa karfe shida. Haka dai ta yi ta bin abin da ta ga ana yi, har lokacin barci. A sannan ne ta samu damar kwashe kayanta da ke cikin (Ghana Must Go) ta jera a loka, kamar yadda ta ga kowa ya yi. Yaran nan makotanta suka fito da wani irin abu cikin kwali da ba ta taba gani ba suna ci, suna korawa da lemon gwangwani suna hira da Turanci, suna kallonta, ita da kullin kayan kuli-kulinta suna ta dariya. Duk ta bi ta sha jinin jikinta, amma ba ta daga kai ta kalle su ba, ta jika ramarta cikin 'yar robarta ta ajiye akan lokarta tana jira ta jiku ta kwada da kuli. Tana ganinsu har lekowa suke da kai suna leka robar ta, amma ragowar jama'ar da ke dakin ba ruwansu da ita, kowa gararin gabansa yake yi. Ta rasa dalilin wadannan yara na sa mata ido da wulakanci a gare ta, daga baya ta fuskanci daya sunanta Nabilah, daya kuma Kausar. Ta kwada ramarta ta ci ta koshi, ta sha ruwa ta kwanta a katifarta da ko zanin gado babu. Ta rufa da zanin atamfar Innarta, wadancan yaran kuwa irin bargonta da hedimasta ya cinye suka rufa da shi. Hatta filon ya dauke ya cinye saboda rashin tsoron Allah irin nasa. Aka yi (light-off) na gabadayan hostel din, ta shafe jikinta da addu'o'i ta kwanta. Washegari da aka yi sallar asubah ta ga kowa yana bin layin wanka, don haka ita ma ta bi ta yi wankanta ta yi sallah a masallaci tare da Imam. Daga nan aka tafi aji. Suna shiga aji ta ga mutanenta sun dauke bencin gabadaya sun maida shi wurin da ba kowa sun zauna, sun kuma kira wata yarinya sun zaunar da ita a wajenta. Ta rasa inda za ta zauna, ta koma karshen ajin ta sanya littafinta daya a kasa ta zauna akai. Zamanta da kamar minti biyar Uncle din ajin ya shigo. Yana ta jefa ido ya hango Mariaman da ya kwana ya tashi da tunaninta jiya, amma bai ganta ba. Gabadaya ajin aka mike, ita ma sai ta mike kamar yadda suka yi, suka hada baki gabadaya suka ce "Good morning Uncle". Ya ce, "Morning class, how are you all?" Suka sake hada baki gaba daya suka ce "We are fine Uncle". Sannan ya yi umarni da a zauna. A sannan ne ya hangota makure a can layin karshe kamar mujiya, kuma a dandaryar kasa. Bai ce komi ba ya bude rajista ya yi kiran lambar kowa, ya amsa, sai a karshe ya ce "No. 40". Shiru ba a amsa ba, a lokacin ya gane lambar Mairo ce, sai ya ce, "Mariama daga yau ke ce no.40". Ta ce "To". Ya rufe rajistar ya dinke fuska sosai, ya ce "Kausar!" Ta amsa, "Yes Uncle". Ya ce "mene ne dalilinki na janye benci ki hana Mariama zama?" Ta yi shiru ba ta amsa ba. Ya dubi dalibar da suka zaunar a wajen, "Ke Laila ina wajen zamanki? Me ya kawo ki nan?" Ta yi saurin mikewa ta koma wajenta. Ya ce "Kausar fito nan". Ta fito tana gatsina ita a dole ga 'yar masu kudi. Saura kadan ya zabga mata mari, sai dai ya yaki zuciyarshi ga yin hakan, ya ce ta fita waje ta yi kneel down, har zuwa lokacin break. Ta cika ta yi fam, kamar balam-balam, dama ga ta buleliya. Ta zobara baki, ta ce "Ai ba ni kadai na janye bencin ba, har da Nabilah". Nabilah ta ce "Wallahi Uncle babu ruwana, ita ce ta ce wai ba zata zauna da billager ba". Bai yi mamaki ba, sai ya bude murya yana tambayar 'yan ajin "Shin dama akwai banbanci tsakanin musulmin kauye da musulmin birni?" Suka ce "A'ah Uncle". Ya ce "To me ye laifin wannan yarinya da kuke kyamarta?" Wasu daga ciki suka hau matsawa suna cewa "Ta zo ta zauna a kusa da mu". Amma Uncle sai cewa ya yi, babu inda zata zauna sai bencin su Nabilah, don haka idan Nabilah da Kausar baza su zauna tare da Maryama ba, sai dai su koma gidan ubansu. Mairo dai na sauraron ikon Allah. Tana tunanin yadda ta ke abar so a wurin Innarta da Babanta, amma wai yau ake takaddama akan inda za ta zauna sabida ita an ga alamar ba ta da arziki. 7/28/21, 10:59 AM - Buhainat😝: 30 A lokacin ta ji wata zuciya na shigarta (determination) akan rayuwa. Ta alkawarta wa ranta idan ilimi na kawo arziki, to zata neme shi ko don 'ya'yanta. Za ta nemi ilimi har sai ta ga karshensa, idan har ana gani. Ba zata so a yi wa danta irin wannan wulakancin ba. Uncle ya lura Mairo kuka ta ke yi, sai zuciyarsa ta karye. Don haka tunda ya gama kiran lambar sai ya fita, bayan ya tabbatarwa Kausar kada ta sake ta bar kneel down din da yasa ta har sai ya dwo. Malamin maths ya shigo ya fara ba su darasi, Mairo ta tattara hankalinta akan malamin gabadaya, ba ta damu da hararar da Nabilah ke mata ba. Ya gama ya fita, sai ga Uncle ya dawo wanda kuma shi ne yake daukarsu darasin Turanci. Yana koyarwa, amma rabin hankalin sa na kan Mairo. Ya lura sabanin ragowar ‘yan ajin, Maryama ta ba shi dukkan 'attention' dinta, da wani muradi cikin kwayan idanunta. A zahiri wannan yarinya bakauyiya ce lakadan, amma ga dukkan alamu, ba haka Allah Ya yi nufin barinta ba. Ya kammala darasinsa ya ba da aiki 'Essay Writting' mai take guda uku, ya ce kowacce ta zabi wanda za ta iya yin sharhi a kansa. A rubuta a kawo masa washegari. Hankalin Mairo ya tashi, domin dan ilimin nata bai kai nan ba. Magana ce ake so su rubuto da harshen Turanci akalla shafi daya da rabi na littafi. Aka kada kararrawar fita break, amma Mairo ba ta yi niyyar fita ba. Ta kurawa aikin 'assignment' dinta ido tana tunanin ta inda za ta bullo. Ba ta ankara ba ta ji wani sassanyan kamshi na dukan hancinta da kuma alamun zaman mutum a bencin gabanta. Ta dago a hankali tana kallonsa, Uncle ne. Ya ce "Yaya dai Maryama, kowa ya fita cin abinci, amma ke ban ga alamar kina da niyyar fita ba?" Ta sadda kai cikin kankanuwar murya ta ce "Ina tunanin yadda zan yi aikin da ka bayar ne". Ya yi murmushi ya ce "Aiki ne kuwa mai sauki, amma ga wanda ya gane tambayar. Wacce tambaya kika dauka a ciki?" Ta sunkuya tana kara nazarinsu, ta ce "Ina ganin ta daya za ta fi mun saukin amsawa, tunda daga karkara na ke, 'Yadda ake bikin sallah a karkararmu". Ya yi murmushi, ya ce "Ni kuwa sai na ga tambaya ta biyu zata fi dacewa da ke 'Ranata ta farko a sakandire', za ki kawo 'points' sosai wanda zai taimaka ki yi 'scoring' maki mai yawa. Kinga sauyin abubuwa da dama, a zuwanki babbar makaranta. Haka ne ko ba haka ne ba?" Ta yi murmushi, wanda ya lotsa kumatunta hagu da dama. Akwai wani asirtaccen kyau a tare da Mariama, wanda rashin gyara da rashin gogewa ya boye shi. Yarinya ce kamar diyar Larabawa, sai dai fatarta a dafe ta ke, kamar an shafa mata shuni, wanda kai tsaye ya banbantata da sauran yaran makarantar. Ta ce "Haka ne Uncle. Na gane cewa, ashe mu ba mutane ba ne, ababen kyama ne ga wasu jinsin al'ummah. Abin dariya ga wadanda Allah Ya yiwa falalar rayuwa. Ban san cewa ni 'yar talaka ba ce sai yanzu, tunda kuwa ban taba neman abin da zan ci na rasa ba, sai na dauka iyakarta ke nan. Ashe akwai masu shi fiye da ni, amma idan da ace ni ce a matsayin mai shi din, ba haka zan yi wa mara shi ba!". Mamakin kalaman karamar yarinya kamar wannan ya kama shi. Sai dai ya kula magana ta ke tun daga karkashin zuciyarta, ba wai tunaninta ba ne. Ya ce "Mariama!" Ta dago ta dube shi, amma ba ta amsa ba. Ya ce "Ina son ki sa wa ranki cewa, ba duka mutanen da kika tarar halinsu daya ne ba. Kowa da kika gani a duniya da irin halayyarsa. Wani yasan darajar kansa, yasan ta mutane, wani bai san darajar kansa ba, bai san ta mutane ba. Wani yasan darajar kansa bai san ta mutane ba.To wannan ba cikakken mutum ba ne, kuma shi ne wanda Allah Ubangiji Ya yi alkawarin dankafar da shi a duniya da lahira sabida girman kansa. Da zarar ka yi tunani ko ya ya cewa, kai wani ne, to kai ba kowa ba ne a wurin Ubangiji. Sabida haka a yadda kika dau kan naki a ba kowa ba, ci gaba da hakan. Amma kada ki yarda da cewa, sai wun fi ki ne. Ido biyu gare su, kunne biyu, kafafu biyu, hannaye biyu, ke ma su gare ki. To akan me za ki yi tunanin sun fi ki? Wanda ya fi ki kawai shi ne wanda ya fi ki tsoron Allah!”. Jikinta ya yi sanyi, ranta ya yi fari. Tana dubanshi da kyawawan idanunta, ta ce "Uncle kana nufin ni ba abun kyama ba ce?" Ya girgiza kai "Ko daya Maryama. Da za ki daure ki fidda su a gabanki ki yi karatu sosai ki dinga gyara kanki, sai kin fi su kyan gani. Ko a yanzu haka kin fi su, gyara suka fi ki. Ba kawa kika zo nema ba, ilimi kika zo nema, irin wanda suka zo nema. To akan me za ki damu da su? Ai abu daya za ki damu da shi, shi ne ki dage ki ga cewa ba su fi ki kokari ba". Ta yi murmushi ta ce "Uncle kana da kirki, sai na ke jinka kamar Yaya Habibu. Shi ma haka yake yi min irin maganganunka. Da zai zo ya ganni a makarantar nan, ban san irin farin cikin da zai yi ba". Ya ce "Yaya Habibu yana ina yanzun? Ni kuwa inje in gaya masa, ga ki a babbar makaranta". Ta washe baki ta ce "Ayyah, yana da nisa, yana karatu ne a kasar waje, amma komi nake yi sai in yi ta ganin kamar yana kallona, sabida shi ne ya dage, ya sani a makaranta". Ya ce "Ni kuwa gani na dage da yardar Allah sai kin yi karatun da Yaya Habibu zai dawo ya yi alfahari da ke, amma hakan ba zai yiwu ba sai da goyon bayanki Maryama, wanda ba komi ba ne da ya wuce perserbearance (jajircewa) da ba da himma". Ta sake yin murmushi har kumatunta suka lotsa, ta ce "Na gode Uncle, kuma na yi maka alkawarin I'll persebere". Ya yi mata tafi guda daya ya ce "Good Maryama, ina neman alfarmar ki rike ni a matsayin Yaya Habibu",. Wani farin ciki ya bayyana a fuskarta, ta ce "Kenan ka yarda na rinka kiranka da Uncle Habibu?" Murmushi ya yi, "A'ah, UNCLE JUNAIDU. Sunana Junaidu Galadanchi". Ta ce "Galadanchi?" Ya ce "Eh, kin santa ne?" Ta ce "A'a, ban taba ji ba ne. Garinku ne Galadanchi ko sunan Babanka ne?" Da alama Maryama matambayiya ce, kuma matambayi ba ya bata. Hazakar yaro na da alaka da yawan tambayarsa (curiosity). Ya ce "Galadanchi karamar unguwa ce a cikin birnin Kano. Sai dai tarihinta mai girma ne ga Kanawa. Duk wani Ba-Kano ya san Galadanchi, sannan mu 'ya'yan cikinta muna alfahari da ita da kasancewarmu 'ya'yanta. A Galadanchi ne aka fara samun Dr. a ilimi a jihar Kano. Haka idan kika bi tarihin manyan 'yan bokon Kano, da mayan malaman Jami’ar Bayero, wadanda suka fito da jihar Kano a tsakanin jihohi 'yan uwanta, to duk 'yan Galadanchi ne. sannan gasu da kyau, ga Alkur’ani da Tajwidi a cikin kansu". Ta ce "Ina fatan wata rana, in ziyarci Galadanchi". Murmushi ya yi "Insha Allahu za ki je Galadanci Maryama. Yanzu dai jeki ci abinci kamar sauran dalibai, idan kun fito 'pref' da yamma sai ki rubuta aikin gobe ki kawo mani". Ba musu ta mike ta nufi kofar fita. Bai daina kallonta ba har sai da ta kule ya daina ganinta. Shi kam bai san dalilin da ya sa ya damu da yarinyar ba. Haka dan zaman da suka yi a yanzu ya kara sanya mishi jin son taimakonta. Mairo da ta fito 'pref' ta yagi takarda kamar da wasa, ta soma rubuta 'essay' dinta mai taken 'My first day in secondary school'. Da jagwalgwalallen turancinta mara 'tenses' har haduwarta da Uncle a aji ta rubuta, inda ta ce, ba ta taba haduwa da mutum mai kirkinsa ba. A karshe ta ce “shin ko mutum nawa ne masu jin kai irin UNCLE JUNAIDU? Ta ce, Uncle Junaidu ya sa mata burin son zama malamar makaranta, wanda a da ba ra'ayinta ke nan ba. Ta sake bin jagwalgwalonta ta yi dan gyaran da zata iya, ta sanya a tsakiyar littattafanta. Washegari da karfin gwiwarta ta shiga aji, to amma Uncle bai tambayi 'assignment' din shi ba sai da period dinsa ta shiga. Yana bi daya bayan daya yana marking har ya zo kan na Maryama Bedi. A zahiri duka 'yan ajin sun fi ta iya Turanci, da kula da 'tenses' sabida su sun sami kyakkyawan tushe daga makarantu masu tsada. To amma idea da ke cikin rubutun Maryam fasaha ce tsagwaronta. Ta yi rubutunta kamar da gasket, tana magana kamar akan idonsa abin ya faru. Ya kirata yana nuna mata kura-kuranta, tare da cewa "Matsalarki daya ce a Ingilishi (tenses), don haka darasinmu na yau tenses ne". Nan da nan ya fara darasi inda Mairo ta dauki dukkan hankalinta ta likawa Uncle. A yau da aka fita break ma ba ta yi saurin fita ba, ta zauna ne tana aikin lissafi (maths). Uncle Junaid ya kwankwasa desk dinta, ta yi hamzarin dagowa kamin ta yi murmushi ta ce "Uncle dama ba ka fita ba ne?" Ya ce "A'ah na fita, dawowa na yi. Tun daga staff room na hango ki kina rubutu, zuwa na yi na gaya miki ki daina zama cikin aji yayin da kowa ya fita. Komi na makarantar nan cikin tsari yake, yanzu lokaci ne na cin abinci ba na yin aiki ba. Idan wani bai ga abinsa ba yana iya cewa ke ce". Ta rufe littafin ta mike ba tare da ta ce dashi komi ba. Ta nufi hanyar fita, har ta kai bakin kofa ya ce, "Maryama". Ta juyo cikin damuwa, ya ce, "Ina fatan ba ranki ne ya baci ba?" Sai ta koma dariya, ta ce "A'ah Uncle". Ya ce "To mai yasa kika yi shiru?" Ta ce "Ka yi hakuri Uncle Junaidu". Ya yi murmushi ya bi hanyar kofa shi ma ya na kissimawa a ranshi Maryam na daga cikin miskilan yara. Cikin sati biyu kacal Mairo ta fahimci tsarin komi na makarantarsu, sai dai ma ta nuna wa wani. Babu ruwanta da su Kausar, duk kuwa da basu fasa yi mata izgilanci ba, a daki ne ko a aji. Sai dai su kansu sun san akwai wani aminci, ko kuwa shakuwa ta musamman tsakanin Maryam da Uncle, don haka basa yi mata a gabansa. Saboda Maryam Uncle Junaid ya kirkiro tutorial class da yamma da yake yi akan darasinsa English da darasin Uncle Wahhab (mathematics), wanda ba karamin taimakawa Mairon ya yi ba. Duk wasu matsalolinta akan karatu Mairo ba ta shayin gayawa Uncle Junaidu shi kuma ya tsaya mata kamar Yayanta. Shi kansa bai san mai yasa ya tsani Kausar da Nabilah ba, tun daga ranar da ya lura sune kawai matsalar Maryama cikin makarantar. Ita kuwa kullum kokarinta shi ne, ta boye abin da suke mata, kada ya gane. Don duk ranar da ya hora su sabida ita, idan sun koma daki akanta suke hucewa. Rannan da ya sa su noma sabida sun karya bencin ta karfin gaske, duk don kada ta zauna kusa da su, da suka komo hostel suna ta digar da gumi. Sun yi jawur sabida wahala, Kausar ta yi kuka ta ce "Wai Nabilah wannan bakauyar kanwar uban Uncle ce ne?" Nabilah ta ce "A'ah, ina jin tare aka haife su, don shi ma da alama dan talaka ne ya soma daukar albashi ya je ya sayo gwanjo yana zanzarewa". Kausar ta ce "Uban wa ya gaya miki? Abokin Yayana ne tare sukai karatu, dan chief justice Atiku Galadanchi ne. Har gidansu na sani sanda muka zo Kano daga Jos da Yaya Yusuf bikin wani abokinsu, abin da na kasa ganewa shi ne, mai wannan billager din ta ke gaya masa yake damuwa da ita? Ni kam da nasan har da irin wadannan a makarantar nan ai da ban yarda Daddy ya kawo ni ba". Nabilah ta ce "Ke kika ga zaki iya, amma ni nan idan an yi hutu bazan dawo ba, Edcel collage zan koma. Minjibir ta rube, ta zama ta yaku-bayi". Suka kwashe da dariya, Mairo dai na jinsu ba ta dago ta dube su ba, sai rubutunta ta ke kamar alhudahuda. Ranar ziyarar 'yan makaranta, wato bisiting day ta zo. Kowanne dalibi ya sha wanka ya yi fes, ya fito neman nasa. Mairo dama ba ta sa a ka ba, tasan Babanta da Innarta duka ba su san da wata ranar ziyara ba. Tunda ko radiyo ba su damu da su saurara ba, don haka ta samu can wani gefe gindin wata bishiyar goba mai inuwa ta zauna akan benci tana nazarin littafin the boy slabe da ta karbo a library. Can anjima ta daga kai ta kalli motoci na gani na fada da ke ta fakin yara na rugawa su rungume iyayensu, sannan a soma kokawar fito da manyan ma'adanan abinci da katon-katon na kayan masarufi ana ajiyewa. Waje ya cakude kowa na nemawa 'yan uwansa wurin zama, babu wanda yasan da ita, a lokacin ne ta ji babu dadi, ta ji kewar Innarta. Idanunta suka cicciko da kwalla. Kamar daga sama ta ji muryar Uncle a kanta ya ce. "Mariama". Da sauri ta dago tana kokarin boye kwallar idonta, Uncle ne rike da manyan ledoji guda biyu, a bayansa wata yarinya ce budurwa da akalla zata girme ta da shekaru biyu da kuma wani yaro da zai yi tsara da ita, su kuma niki-niki da manyan kulolin abinci da picknick cooler wato irin kular nan da ake zuba lemuka da kankara mai hade da dan famfo a jiki. Ko ba ta tambaya ba tsabar kamanninsu da juna ya gaya mata wadannan yaran kannen Uncle Junaid ne. Ta zame kasa tana gaishe shi, ya ce "Kuka kike ko Maryama, sabida mene?" Ta share kwallar idonta dai-dai lokacin da shi da budurwar suka zauna akan bencin nata, ta ce "Lah Uncle ba kuka nake yi ba". Ya ce "Mai yasa 'yan gidanku ba su zo ba?" Ta ce "Ba su san ana yi ba". Ya ce "To ki fada min adires na garinku ni da kaina zan je na taho da su a bisiting na gaba. Yanzu dai ga kannena Ilham da Sagir sun zo miki bisiting, are you o.k?" Farin cikinta ya gaza boyuwa, bakinta ya gaza rufo don dadi. Ba tasan mai zata ce da Uncle Junaid ba, sai ta kama hannun Ilham tana murmushi, ta ce, "Na gode Ilham". Ilham ta ce "Ba komi Maryam, yadda Yaya Junaid ke ba ni labarinki sai na dauka zan ga wata babbar budurwa, ashe kamar Sagir ce Maryama?" Ya mike yana cewa "Ki tabbata ta ci abincin, kuma ba ta yi kewar kowa nata ba, I know you Ilham. Zan dawo nan da awa daya mu tafi". Ta ce "To Yaya Junaidu". Tana murmushi. Ilham ta ce "Amma ko kannenki ba su zo ba Maryam?" Ta ce "Ba ni da kanne, ni ce auta a wurin Innata". Suka ci gaba da hira, Ilham na kokarin cika umarnin Yayanta na ganin cewa, ba ta bar Maryam da kewa ba kamar yadda dan uwanta ya umarce ta. Ta zuba mata abinci mai rai da motsi cikin filet da kirjin kaza ta mika mata tana cewa "Ci maza kamin Yaya Junaidu ya dawo ya tuhume ni da barinki da yunwa". Dariya ta yi, da ta lotsa kumatunta, tana tambayar kanta ko wane matsayi Uncle Junaid ya ba ta haka a wurin 'yan uwansa? Girmansa da kimarsa ya karu a zuciyarta. Tana ganin bayan Baba da Inna da Yaya Habibu ba ta da kamar Uncle Junaidu. Ya dawo da wata leda mai dauke da ruwan (Faro) roba uku masu sanyi ya mikawa Ilham. Suka sha dukkansu sannan suka yi haramar tafiya, Mairo ta ji babu dadi. Cikin 'yan awoyin da ta yi da Ilham sun saba sosai. Ta bude baki cikin al'ajabi tana kallon Uncle da ya ce duka wannan kayan nata ne. Abinci kuma daga mahaifiyarsu ne sai ta rasa irin godiyar da zata yi wa Uncle din nata. Bayan tafiyarsu ta kinkimi kayanta daya bayan daya ta nufi hostel. Cikin ledojin ba komi ba ne sai biskit na kwali kala-kala da crackers na shan shayi irin wadanda ta ke ganin su Kausar na ci, dayar kuwa alawoyi ne, cakulet kala-kala masu dan karen tsada da katon na irin taliyar da ta ga dalibai suna jikawa (indomie), sai katon na lemon gwangwani (Rani). Baki ta bude cikin matsanancin firgici, ba ta taba tsammanin wai ita Mairo zata taba cin irin wadannan abincin ba a rayuwarta. Cikin kulolin kuwa bayan abinci akwai soyayyun kaji wadanda suka soyu rakau yadda za su jima ba su lalace ba, cin-cin mai nama (meat pie), cake da sandwitch masu yawa sosai. Kenan godiya ga Uncle Junaid wadda ba ta karewa. Mutanenta suka shigo, wani abin mamaki kulolinsu duk iri daya ne da nata, sai kala da ta banbanta. Suka yi kasake! Cikin mamaki ganin irin garar da ke gaban Mairo wadda ko a mafarkinsu ba su zata ba. Abin da suka dauka shi ne, ramar da ta ke kwadawa mai tsamin tsiya da kanzo su za a karo mata. To sai ga sabani ga tunaninsu, ina ruwan Allah Mai azurta bawa. Mairo dai jeren kayanta ta ke a loka, ba ta kula su ba. Nabilah ta kasa shiru ta ce, "Kausar yau billager ta shigo gari". Kausar ta ce "Ke ina jin 'charity' ne daga (MSS), ba ki san ta shiga MSS ba? Kungiyar 'yan a bamu saboda Allah?" Ita yaran sai suka koma ba ta dariya sabida yadda suka sa mata ido babu gaira babu dalili, ko mai ya yi masu zafi da ita? Allahu A'alam. Bayan bisiting da sati biyu, rannan Mairo ta fito domin yin fitsari da daddare a lokacin Kausar ma ta fito ta tsugunna a bakin rariyar hostel tana goge bakinta domin ta kwanta. Mairo na daga bandaki ta hangi wani mulmulallen abu mai sheki da tsayi na sanda ya nufi Kausar. Ta ware idanunta gabadaya sai ta gane katon maciji ne wanda ake rade-radin akwai a makarantar. Ta yar da butarta ta sheko da gudu dai-dai sanda macijin ya fasa kai, ta angije Kausar tun karfinta ta wulwula ta fada kwatami da baka, abin tsautsayi, sai kulbar (macijiyar) nan ta huce fushinta a kafar Mairo, wato ta sare ta. Kausar ta mike cike da bala'i a lokacin idanunta suka gane mata abin da ke faruwa, dai-dai lokacin kulbar ta sulale tana komawa inda ta fito, ga kuma Mairon da ta angije ta kwance a kasa ba yadda ta ke. Ta daura hannuwa aka ta rafsa ihu, wanda ya ratsa gaba dayan hostel din, student da metron suka fito. Kausar ta ce “macijiya ce ta sare ta.” Ai jin haka captain ta suri Mairo, sauran yara suka bi ta yuuu! Har da su Kausar sai gidan principal ana buga mata kofa. Ta fito a gigice ita ma nan take ta bugawa school doctor waya, nan da nan sai ga ta, aka wuce da Mairo asibitin makaranta, Doctor ta dukufa ga son ceto ranta. Kausar da Nabilah suka kasa komawa hostel ko babu komai akwai tausayin rai a zukatansu, balle ita Kausar da tasan hakikanin yadda abinda ya faru. Nadamar abubuwan da ta ringa yi wa Maryam Bedi, suka shige ta. Ta ji tausayin Maryam matuka, ta kuma tambayi kanta, shin ko wace irin zuciya ce da ita? Irin su Maryam ne masu rama sharran da hairan, babu shakkah ta yi nadama. Nabilah ta yi mamakin damuwar Kausar akan Maryam ta yi yawa, ta kasa ko magana. Ta ce "Kausar kowa ya koma hostel sai mu, ni fa tsoro nake ji". A salube Kausar ta sa kafa cikin dan karamin asibitin ta samu benci ta zauna, ba ta da niyyar tashi. Nabilah ta biyota cikin mamaki, ta ce "Wai me ya faru ne? Ba zaki zo mu tafi ba?" Ta ce "Je ki abinki Nabilah. Amma ni a nan zan kwana". Nabilah ta kama baki, dai-dai lokacin da Mummy Dukku wato principal ta fito zata koma gidanta. Ta hango su Nabilah ta ce, "Ku kuma me kuke a nan ba ku koma hostel ba?" Kausar sai ta sa kuka. Ta matso ta dafa kanta domin ta santa farin sani sabida mahaifinta, ta ce "kawarku ce ince ko?" Nabilah ta yi saurin cewa "A'ah, dakinmu ne kawai daya". Mummy ta lura da kukan da Kausar ta ke sosai ta ce, "Ke kuwa tausayinki ya yi yawa Kausar, alhamdu lillahi dafin bai shiga cikinta ba, kuma Doctor ta zuke shi. Insha Allah zuwa safiya za ta warware, tashi ku tafi dare ya yi sosai". Sai da suka je daki ne Kausar ta ke gayawa Nabilah hakikanin yadda akai maciji ya sari Maryam. Ta ce "Yanzu ni tashin hankalina shi ne, idan ta mutu ban nemi gafararta ba ina zan sa kaina?" Jikin Nabilah ma ya yi sanyi, ta ce, "Allah Sarki, irin su ne ake cewa masu halin 'yan aljannah". Suka yi jugum-jugum har wayewar gari ba su runtsa ba, nadama ta ishe su, sai kuma kaunar Maryam farat daya ta bi zuciyoyinsu. Washegari Uncle ya zo kiran suna kamar yadda ya saba, cike da mamakin rashin ganin Maryama a class don kullum ya shigo idanuwanshi akan wurin zamanta yake. Duk da haka bai fasa kiran sunan ba, har ya zo No. 40, shiru ba ta amsa ba. Ya dago manyan idanunsa ya zubawa Kausar cike da zargi kamar ita ce ta boye Maryaman. Ya ce "dakin ku daya, tana ina ban ganta ba?" Kirjinsa har wani harbawa yake da sauri-da-sauri. Fargabarsa kada ace da shi iyayenta sun cire ta daga makarantar sabida su Kausar. Bakin-cikinsa shi ne yau ace Maryama ta bar makarantar nan. Tashin hankalinsa shine ko sunan kauyensu bai sani ba, alhalin yanzu yadda yake kaunar Ilham haka yake kaunar Maryama. Idan zai iya rabuwa da ita, to hakika zai iya rabuwa da Ilham. Cikin in-ina Kausar ta ce "Maciji ne ya sare ta, tana kwance a maternity..." Tun kamin ta kai karshe Uncle ya fita. Ya doshi maternity cikin matsanancin tashin hankali, ko gani ba ya yi sosai. Ya banka kofar da kafarsa babu neman izini. A kwance ta ke, idanunta a rufe, rana daya kacal ta zabge, ta yi wani irin fari fat kamar babu jini a jikinta, sannan ta kumbura kamar an hura balam-balam. Nurse din da ke kokarin daura mata 'drip' ta juyo a razane ta dube shi, bai kula ta ba ya karisa gaban gadon da Maryam ke kwance ya tsaya kurum yana kallonta. Kamar an ce da ita bude idonki, ko kuma alamar tsayuwar mutum ta ji a kanta oho, ta bude fararen idanunta a hankali wadanda suka kumbura suka yi mata nauyin budewa, a hankali ta ce "Uncle…….." Sai hawaye suka zubo ta gefen idonta. Ya yi saurin kama hannun damanta, ya ce "Sannu Maryama, sannu kin ji. Allah Ya ba ki sauki". Ya juya ga nurse din ya ce "Edcuse me madam Serah, na yi miki shisshigi cikin aikin ki. Maryam na daga cikin dalibai na masu muhimmanci a gare ni. Ki yi hakuri". Ta yi murmushi ta ce "Ai na ga alama, wannan patient din taka akwai raki da saurin kuka. Na dauka dadi zaki ji da kika ga Uncle sai kuma ki kama kuka?" Mairo ta maida idanunta ta rufe tana murmushi. Ta nemi ciwon da jikinta ke yi ta rasa, sabida kasancewar Uncle Junaidu tare da ita. Suna magana a kanta shi da Madam Serah ta gaya mishi wannan macijiya ta dade tana sarar dalibai, anyi duk iya kokarin da za a yi don ganin an fitar da ita daga makarantar an rasa. Wani zubin sai a yi tsammanin ma ta mutu don sai a yi shekaru biyu ba a ji duriyarta ba. Amma yanzu kam za a daukaka zancen zuwa federal da yardar Allah za a fitar da ita. Ya ce "Maryama ta kumbura, ta yi biyun yadda ta ke". Ta yi murmushi ta ce "Jini ne babu isashshe a jikinta, wanda aka zuke tare da dafin amma already an tafi a sayo wanda za a sanya mata a asibitin Aminu Kano". Hankalin Uncle ya tashi, ya ce yana son ganin Doctor Nanah, ta ce tana ofis ka karisa. Ya samu Dr. Nanah a ofis cikin tashin hankali. Ta ce "Yaya dai Uncle Junaidu?" Ya ce "So nike ki debi jinina idan ya yi dai-dai ki sanyawa student dina". Ta ce "To bari in diba kadan a auna a gani". Ta zuka kadan a sirinji ta mikawa lab asisstant ta auna, ya nuna (negatibe), ga duk wasu gwaje-gwaje da akayi, sannan dukkansu a 0+. Ya kwanta ta debi leda biyu ta ce ya ci gaba da kwanciya ya huta. Ta ba nurse ta sanyawa Mairo ta dawo tana fada mishi irin abincin da zai ringa ci har zuwa kwana bakwai. Nan da nan labari ya watsu cikin FGGC cewa Uncle Junaid ya yi donating jini wa Maryam. A'ah, cece-kuce ya soma (round) zagaye makarantar musamman daga 'yan ajinsa da daman suna hankalce da su. Yara kanana da su amma sun iya gulma. 'Yan manyan aji kuwa masu yi masa asirtacciyar soyayyah, wadanda a da ba su san da Maryam din ba suka zo suna kallonta, duk ta takura ta rasa inda zata sa kanta, balle da ta lura har da masu yi mata mugun kallo. Ranar da ta dawo hostel Kausar kunyarta ta ke ji, ko ido ta kasa hadawa da ita. Daga baya da ta ga Maryam din ma ba ta damu ba harkar gabanta kawai ta keyi, sai ta zo bakin gadonta ta zauna ba ta ce komai ba. Nabilah ta shigo itama ta zauna a katifarta abin da ko da wasa ba su taba yi ba. Suka ce "Don Allah don Annabi Maryam ki yafe mana. Wallahi sharrin shaidan ne, kuma mun gode da sacrifice (sadaukar da kan) da kika yi mana. Muna rokonki daga yau mu zama daya a makarantar nan, wato mu zama mu uku cikin amana". Mairo ta yi murmushi ta ce "Babu komi, ni dama ban taba kullatarku ba, mamaki dai kuke ba ni. Amma shi ke nan, komi ya wuce". Daga ranar Maryam, Nabilah da Kausar ba a kara jin kansu ba. To sai kuma ciwon ciki ya kama Kausar, kullum ba ta iya barci, sai murkususu da kuka cikin dare, haka suke kwana tsaye a kanta har asubah sannan zata samu barci. Da suka ga abin ya fi karfinsu sai suka yi reporting ga hukumar makaranta. Aka dauki Kausar zuwa maternity inda aka gano kabar ciki ke damunta. Nan da nan aka yi hamzarin mikata gida, domin abin ya fi karfin asibitin makaranta. Suka koma kewar Kausar tare da yi mata addu'a, kullum, har lokacin jarabawa ya matso. Kokarin Uncle shi ne Maryam ta saki ranta ta yi abin kirki a jarrabawarta, amma ina! Tunanin Kausar da halin da ta ke ciki ya hanata zama lafiya. Ranar da suka soma jarrabawa suka dawo hostel sai suka ga babu ko allurar Kausar a dakin. Captain da Metron sun kwashe sun bai wa iyayenta. A gigice Mairo ta fita kafarta ko takalmi babu, kanta babu kallabi. Nabilah ma ta bi ta dakin Metron suna tambayarta yaushe aka kwashe kayan Kausar? Ta ce "Allah sarki, wannan yarinyar diyar Gwamnan Jos, ta rasu. Tun satin da ya wuce". Suka rushe da kuka, suka zube anan suna ta yi. Tsoron Allah Ya kara shigar Maryam da Nabilah. Tun daga ranar suka koma wasu irin sukuku, ba fuss ba ass. Shi kansa Uncle ya girgiza da mutuwar Kausar, ya yi ta lallashinsu yana ba su baki. Ya ce da Nabilah abin da yake ankarar da ita ke nan kan daukan duniya da zafi. Shi Ubangiji ba ruwansa da ko kai wane ne, dan wane ne, wane ne ubanka face ayyukanka kyawawa. Nabilah ta fi Maryam ramewa, ta fi ta gigicewa, domion dai ta fi ta shakuwa da Kausar. Sannan ta kara rungumar Maryam a matsayin 'yar uwarta don sai ta ke ganinta kamar Kausar. Aka yi jarrabawa aka kare, sai hutu sati mai zuwa. Sai dai fa daga Maryam har Nabilah kowacce cike ta ke da zullumin sakamakonta. Uncle ya yi fushi da Maryam sosai, domin ta dauko na talatin da takwas yayin da Nabilah ta dauko na arba'in. Ta kaskantar da kai ta dinga ba Uncle hakuri, ta tabbatar masa zango mai zuwa za ta dage ta yi abin da zai ji dadi. Mutuwar Kausar ke nukurkusarta har zuwa lokacin. Ranar hutu malam Bedi sammako ya yi domin hedimasta ya gaya masa tun ana saura kwana uku, don haka a kwanakin nan barcin da suka yi kalilan ne sabida dokin dawowar Mairo. Barin ma Inna Hure da shiga goma, fita goma sai ta siyo abin da zata ajiyewa Maironta. Tun daga kan goriba, kurna, goba, magarya, dinya da ire-irensu wadanda tasan Mairon na so babu wanda ba ta nemo ta ajiye mata ba. Duk sammakon Baban Mairo bai isa makarantar ba sai da aka soma dadewa. Mairo da Nabilah na zaune karkashin dalbejiya dukkaninsu cikin damuwa suke na rashin ganin kowa nasu. Nabilah ta ce "Da na san gidanku Maryam da na zo kamin na wuce Lagos hutu wurin Auntyna". Maryam ta jinjina kai ta ce "Ba zaki iya zuwa gidanmu ba, can ne cikin surkukin kauye, cikin Fanshekara". Nabilah ta ce "Don ba kisan yadda nake son zuwa kauye ba ne, idan kuma kin musanta hakan ki gaya min ki gani". Ta dauko biro da jotter tana jiran ta bakin Mairon. Mairo ta ce "Fanshekara, motar Gurin Gawa, idan an shiga Gurin Gawa, sai a tambayi gidan Malam Bedi kowa ya sani. Idan kuwa yara ne kika ce musu 'MAIRON HURE' da gudu za su rako ki". Duka Nabilah ta dauke cikin jotterta, wanda ke bayansu ma ba su san da tsayuwarshi ba shi ma ya dauke cikin kakkaifar kwakwalwarsa. "Lah, ga Babana nan!". Mairo ta fada cikin matsananciyar murna, kamin ta kwasa da gudu ta rungume Malam Bedi. Nabilah ta dago daga rubutun da ta ke ta bi bayan Mairo da kallo, sai ta hango ta rungume da wani yagulallen tsoho, sanye cikin yadin algarara, kanshi duk furfura. Ta ce a ranta, "Ya za a yi ace wannan ne ya haifi Mairo? Ya fi kama da kakanta fiye da babanta". Ba tasan cewa ba wai shekarun da ya yi a duniya ba ne suka janyo masa wannan tsufan ba, a'a, wahalar rayuwa ce kawai ta noma, girbi, da sussuka irin ta kowanne manomin kauye. Tausayin Mairo ya kamata, ta tabbata ita 'yar talaka ce futuk, amma she is contented with what she habe (a gamshe ta ke da abin da ta ke da shi, ba ta taba kwadayin abin hannun wani ba). Mairo ba ta taba tambayar Nabilah ita 'yar waye ko daga ina ta fito ba. Wannan ya sa Nabilah tambayar kanta, shin Maryam wace iri ce? A zahiri miskila ce, abin da tasa a gabanta shi ne kawai ya dame ta. Ta mike ta tadda su tana gayas da Malam Bedi cikin tsananin girmamawa. Mairo ta ce "Baba Nabilah sunanta, ajinmu daya, dakinmu daya. Da har da Kausar amma ita ta rasu". Fuskarshi ta nuna bai ji dadi ba, ya ce, "Sannunki Nabilah, Allah Ya jikan Kausar". Idanunta ya ciko da hawaye, ta juya tana sharewa ta ce, "Amin". Babu irin neman da ba ta yi wa Uncle ba, don su gaisa da Babanta, amma ba ta ganshi ba. A haka cikin rashin jin dadi ta yi sallama da Nabila rike da 'yar jakar kayanta ta buhu (Ghana Must Go) suka fita. Sun sha wuya matuka irin ta motocin haya kamin Allah Ya kawo su gida. Ganin irin wuyar da Babanta ya sha ya sa ta alkawarta wa ranta daga wannan hutun zata hutar da shi kai ta makaranta da dawo da ita, tunda ta gane hanya zata dinga tafiya da kanta. Tunda yaro ya shigo da jakar Mairo Hure ta biyo bayansa da saurinta. A soro suka yi kacibus, da Mairon nata. Suka rungume juna kamin Hure ta soma hawaye ta ce "Ashe wannan ranar zata zo Mairo, ranar da zan kara ganinki?" Mairo kuwa baki ya ki rufuwa a haka suka karasa cikin gidan kamar wadanda suka shekara ba su ga juna ba. Inda duk Inna ta mika hannu sai ta zarowa Mairo abin sawa a baka, ta ci ta yi nak! Ta ci girkin Innarta da ta yi kewa, ba kadan ba. Duk da cewa abin da ta ke ci a makaranta ya fi na gidansu amfani a jikin dan Adam. Hure ta kasa boye mamakinta, ta ce "Shin mai kike ci a makarantar nan ne Mairo? Kinga kuwa yadda kika zama buleliya, kika yi fari sai sheki kike?" Mairo ta sa dariya, ta ce, "Ba abin da bana ci Inna. Tun daga kan kwai, dankali, agada, doya, madara, nama da kifi ba abin da ba a bamu. Har 'ya'yan itace (fruits) ba dole in zama buleliya ba?" A ranar dai Mairo da iyayenta kwanan zaune suka yi, tana ba su labarin rayuwarta a makaranta. Sai dai fa duk rabin hirarta, "Uncle Junaidu" wanda ya yi ruwa ya yi tsaki wurin sama mata farin ciki da walwala a cikin dalibai 'yan uwanta. Malam Bedi ya ce, "To Allah Ya saka mishi da alkhairi". Sai dai a cikin labarinta ba ta kawo labarin saran sa macijiya ta yi mata ba, don ta tabbata idan suka ji, kidimewa za su yi su ce ba zata koma ba. Hutun Mairo gwanin ban sha'awa a gidansu, gabadaya yanayin rayuwarta ya canza, ba ta barin Innarta da aiki ko ya ya, sai ta karba ta yi. Haka ta ke bin babanta gona tana taya shi shuka da ban ruwa. Abokinta Rabe da ya ji ta zo hutu daga makarantar kwanan da aka kai ta, sai ya aiko yaro rannan da yamma wai Mairo ta zo su je su hau tsamiya. Malam na jin sanda ta maida dan aiken ya tambayo mata Rabe, shin yanzu ta yi masa kama da 'ya'yan birrai ne da zai ce ta zo ta hau bishiya? Sai ya yi murmushi yana kara shi wa Habibu albarka a zuciyarsa. 7/28/21, 4:41 PM - Kawata: 4999 *** *** Uncle Junaidu ya yi mata halarcin da ba zata taba mantawa ba a rayuwarta. Tare da shi aka yi ta zaman makoki har tsayin kwanaki bakwai, mahaifiyarshi da kannenshi duka ya kawo su sun yi wa Inna Hure gaisuwa. Ranar da aka yi sadakar bakwai ya tura aka kira masa Mairo azure, ya kara yi mata ta'aziyya, ya kara da nasihu masu sanyaya rai da karfafa gwiwa. Ya ce ta daure sati mai zuwa ta dawo makaranta har zangon ya yi nisa ba tareda ita ba. Ta rantse masa zata dawo amma tana tausayin Innarta, yadda zata barta cikin kewa. Ya ce "Wata rana aure zaki yi Maryama, ke da Inna sai gani da yawo, ita kanta tasan hakan. Don haka ki taimake ni in rike nauyin da marigayi ya aza mani akan karatunki". Bayan tafiyarsa Mairo da Innarta idan ka gansu gwanin ban tausayi. Tunanin Mairo shi ne, wa zai dinga nomawa Innarta abin da zata ci? Idan wanda ke cikin rumbunsu ya kare? Allah maji kan bawa, washegari sai ga Alhaji Abbas niki-niki da kayan abinci ya kawo musu. Ya kuma ce, wannan nauyin ya dauke shi insha Allahu. Sai a nan hankalin Mairo ya dan kwanta duk da Innar ma ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba. Shi ma Alhajin ya yi mata zancen makaranta ta ce, insha Allah karshen wannan satin zata koma. Hakan kuwa aka yi, ranar litinin ta yi shiri ta koma makaranta. Nabilah ta yi mata ta'aziyyar babanta wanda ta ji a bakin Uncle Junaidu. Rayuwar Mairo ta sauya kwarai, ta zama babu walwala, akwai shakuwa da kauna mai tsanani tsakaninta da mahaifinta, don haka ta ke jin kanta tamkar ita kadai ta rage a duniyar. Sai ta samu kanta da son yin abin da zai debe mata kewa, don haka ta fara tunanin yin RUBUTU. Tana yi tana gutsirewa ta ajiye, idan ta ji bai yi mata ba. Kamar da wasa, ta fara rubutun labarai cikin harshen Turanci a kalla guda biyar tana yagawa. Lokacin da ta shiga aji biyar na babbar sakandire aka ba ta kallabin 'AMIRA' sabida hidimarta ga masallaci da kungiyar dalibai musulmai da Uncle Junaid ya sa ta. Haka nan ita ce ja gaba a club din Uncle, watau English club. Kowa yasan Uncle Junaid a Minjibir, yasan shi tare da Maryam Bedi. Mairo ce mai rubutawa club din DRAMA Uncle ya yi gyara a gabatar da ita. Wannan wata hikima ce da Allah Ya yi mata wadda ke bai wa kowa mamaki. Sai dai iyaka kwakkwafinka da sa ido, haka nan so kulla karya da sharri, ba zaka ce akwai soyayya tsakanin Junaid da Mairo ba, sai mutunta juna. A wannan hutun na zangonsu na biyun karshe a sakandire da Mairo ta zo gida. Ta tarar da ciwon kafar Inna ya yi tsanani. Ko bayan gida ba ta iya takawa sai dai ta ajiye (foo) a kusa da ita. Don haka Mairo ta kara kadewa ta rame, ta kuma soma tunanin jingine makaranta domin Innarta, tun tana tunanin Habibu har ta watsar ta hakura da shi, shi da ya ce shekaru shidda kacal zai yi. Ta tabbata inda duk Habibu ya ke tunda ya iya ya yi shekaru takwas bai neme su ba, to babu shakka ya manta da su, ya samu sabuwar rayuwa a gaba. Ba zata taba amincewa da cewa wani mugun al'amari ne ya faru da shi ba, tunda kuwa lafiya ita ke buya, amma ba rashinta ba. Cikin watan January ne sanyi ya yi tsanani, hazo ya mamaye sararin samaniya, wanda duk ya yi kuskuren fita babu shakka gashin ido dana girarsa fari fat za su koma. Mairo ta dawo daga wani chemist inda ta amsowa Inna maganin mura tana tafe yafe da mayafin gyauton atamfa, ta dunkule hannuwanta wuri guda.Tana ta sauri domin ta daura dafa-dukar taliya akan wuta, wadda zata bai wa Innar, kasancewar ba komi ta ke iya ci ba, sai abu mai laushi, kuma mai dan ruwa-ruwa, duka Mairo na kokari a kai. Ta kada ta raya da Innar ta kai ta asibiti, amma Innar ta ki, ta ce, ciwon kafa ba a kanta tsoffi suka fara shi ba. Ta doso zauren gidansu ke nan ta hange shi, tsaye a kofar gidansu. Sanye yake da farar shirt (Armani) da dogon bakin wandon jeans ya daura jibgegiyar rigar sanyi mai hade da hula bisa. Duk hazo ya ba ta tsararren gashin idonsa, girarsa da sajensa. Mairo ta ce a ranta, Allah Sarki Uncle! Cikin wannan sanyin ya taho tun daga Minjibir sabida rashin komawata makaranta. Tun daga nesa ta ke yi masa murmushi amma shi fushi yake sosai. Ta kariso cikin nutsuwa, tana karasowa ta russuna tana gayas da shi ya ce "Ni bana son wata gaisuwarki, kawai shiga ciki ki hado kayanki ki zo mu tafi". Ta girgiza kai kamin ta wuce cikin gidan ya bi ta a baya. Ta fara da sauke tukunyar daga kan wuta, kana suka karasa dakin Innan da sallama. Shi kansa ya girgiza da ganin ramar da Innar ta yi, tana kwance bisa katifar auduga ta amsa sallamar su. Nan ya gano amsarsa ta rashin komowar Mairo makaranta. Jikinsa ya yi sanyi, ya daga manyan idanunsa ya dube ta suka yi wa juna kuri da ido. Wani irin tausayinta ke ratsa zuciyarshi, wani sabon feelings ya shiga ratsa kowannensu. A yanzu kam ji ta ke ba ta da kowa sai Uncle, babu wanda ya damu da rayuwarta sai shi. Duk da Alhaji Abbas na iya kokarinshi akansu. Ta sauke kwayar idonta kasa a hankali, hawaye na disa bisa tafukanta. Ya sauke nasa idon akan Innan cikin matsananciyar damuwa, ya ce "Sannunku da jiki Inna, amma ya dace ki daure yanzun nan mu tafi asibiti". Ta ce "Kayya Junaidu, wadannan kafafun bana jin za su kuma takawa a doron kasa. Akwai likitan da ya isa ya raba tsoho da ciwon kafa? Sai Allah!" Ya ce "Inna ku daina fidda rai da rahmar Ubangiji, babu ciwon da Allah Ya saukar, ba tare da ya saukar dashi tare da maganinsa ba". Ta ce "Ai ana shan maganin Junaidu. Watakila abin da nake gudu ne, dole sai ya faru…….." Cikin matsananciyar damuwa ya ce "Wane abu ne kike gudu Inna?" Ta ce "Zaman Mairo da Iyalan Abbas". Daga haka ta yi shiru. Daga shi har Mairo su ma shirun suka yi. Mairo ta rasa dalilin da ya sa Inna ta tsani iyalan Alhaji Abbas, abin kam ya wuce na cewa wai don sun so su dauke ta ne. Watakila dai akwai wani boyayyen abun don yadda ba ta sonsu ba ta shiga shirginsu, haka su ma. Tun tasowarta ba ta taba ganin wata cikin matan Alhaji Abbas a gidansu ba, haka ita ma Innar ba ta taba zuwa ba. Ita duk ba wannan ya dame ta ba, illa samun lafiyar Innarta. Ba ta son jin irin maganganun da Innan ke yi a kullum suna kara tayar mata da hankali. Junaid ya yi musu sallama ya tafi, washegari sai ga shi ya zo da likita har kauyen wanda likitan gidan su ne. Ya dade yana duba kafafun Innar, ya rubuta magunguna masu inganci da allurai ya ba Junaidu. Ranar litinin ya dawo da magungunan ya nunawa Mairo tsarin shan su dalla-dalla. Ya je babban dakin shan magani na kauyen ya tattauna da nurse da kullum zata zo har gida ta dinga yi wa Innan allura. Cikin sati guda kafafun Inna sun yi kyau, har tana iya zagayawa bayan gida. Ranar wata alhamis da daddare suna kwance ta ce "Mairo”, tace “Na’am Inna” “ ni ko ba don wani abu ba, da na ce Junaidu YA AURE KI". Gaban Mairo ya fadi damm! Ta dade bata saisaita tunaninta ba, cikin dabarbarcewa ta ce "Inna ke ko mai yasa kika yi wannan tunanin? Uncle Junaidu Yayana ne, yadda na dauki Yaya Habibu haka na dauki Uncle, babu wani tunani na daban ko ya ya game da shi a zuciyata. Allah ne Ya hada mu, Ya hada zumunci mai karfi a zuciyoyinmu. Babu wani abu makamancin wannan, sai mutunta juna". Inna ta yi murmushi ta ce "Wannan zuciyar Mairo ce kike gaya mini, ba ta Junaid ba. Kin taba ganin inda namiji zai yi ta wahala da mace da iyayenta babu gaira babu dalili? Idan kin ga kare na sunsunar takalmi, wallahi dauka zai yi. Har yanzu ke yarinya ce da sauranki. In gaya miki gaskiya na hango miki abin da ke ba ki hango ba, cikin kwayar idon Junaidu. Na hango miki abubuwa da dama, wadanda a shekarunki bazaki iya hango su ba. Babu komai cikin kwayar idanunsa sai sonki da kaunarki, ke ma sai dai ki karyata zuciyarki da gan-gan, amma kina son Junaidu. Adadin soyayyarka da mutum, yana da nasaba da yawan ambatonsa. To gaya min tun haduwarki da shi, wace rana ce ba ki ambace shi ba? Ni ba wani abu na ce ba, kawai ina gano miki dacewar hakan. Ina gano miki mutumin da zai rike ki da kauna ta gaskiya, har zuwa karshen rayuwarki. Wanda kuma shi ne wannan Junaidun. Duk runtsi, duk wahala da tsanani kada ki bari a rabaku. Zan iya rantsuwa in fada miki Junaidu sonki yake yi, idan kuma ba ki yarda ba, ki jira LOKACI ya fada miki……." Cikin gundura da zancen ta ce "Na ji Inna, amma don Allah don Annabi ki rufa min asiri kada ki ce wai ya aure ni, ai kin zubar min da aji, sai ka ce wata wadda kike neman yadda za ki yi da ita? Ni kam gare ni har gobe Uncle Junaidu Yayana ne". Inna ta yi murmushi ta ce "Neman yarda zan alkinta rayuwarki nake yi mana, ga shi kuma ina hango inda za a alkinta min ke". Ta ce (kamar ta yi kuka), "Ni dai don Allah Inna ki bari……..". Ta ce "Na bari, amma wata rana idan kina shayar da jaririn Junaidu, ki tuna na gaya miki Junaidu na sonki, tun ba ki mallaki hankalin kanki ba". Ta yi narai-narai da fuska, ta ce "Yanzu don Allah Inna ba zaki bar zancen nan ba?" Ta ce "Na bari". Ashe karshen hirar tasu ke nan. Inna Hure ta tako da asubahi cikin dafa bango domin yin alwala, ta zo gittawa ta gefen da rijiyarsu ta ke, santsin cabalbalin gindin rijiyar ya kwashe ta ga kafafun babu karfi, ta zame ta baya sai ji kake cindummmm….! Ta fada rijiyar ita da butar da ke hannunta. Mairo wadda ba ta yi barci ba tun daren jiya, tana tunanin zancen Inna akan Uncle Junaidu, ta kasa yakice al'amarin a zuciyarta. Haka kawai ta samu kanta da fatan ina ma ace zancen Inna ya tabbata gaskiya? Uncle Junaidu ya so ta? Ita kuwa da wace irin sa'a zata yi a rayuwarta? A farkon shekatun karatunta ba ta tantance wane ne Junaid ba, sai da girma da hankali suka fara game mata jiki. Uncle Junaidu na daya daga cikin irin mazan da suka yi karanci a wannan zamanin. Ta fannin sura, halayya da kyawawan dabi'u. Ta kasance ma'abociyar karance-karancen littattafan nobels' na Turanci. Littattafan Shakespear, Wole Soyinka, Zainab Alkali, Abubakar Gimba, Ama Ata Aidoo da mabiyansu babu wanda bata karanta ba. A duk lokacin da ta ke karatun, takan rasa dalilin da yasa ta ke danganta al'amarin jaruman littafin da Uncle da ita kanta. Ba tasan dalilin da yasa a duk lokacin da aka ambaci managarcin mutum mai kyawun sura ta ke cewa cikin ranta, "Kaman Uncle Junaidu". Eh, Junaidu kyakkyawa ne, ma'abocin kwarjini, zati da kamala, wanda kwata-kwata bai dace da matsayin da yake kai ba, wato malamin makaranta. Saidai da yake ance (ra’ayi riga ne) Mutum ne da yasan mene ne 'dressing' wanda kuma kowanne irin kaya ke karbarsa, su dace da da zubin halittarsa. Kai kace don shikadai aka kirkiresu. Junaidu idan ya shigo waje dole kasan ya shigo, sabida kwarjininsa da cikar zati. Yana da fara'a amma yana da zucciya, abu kadan sai ya bata mishi rai, haka abu kadan zaka yi ya wanke laifinka nan take daga zuciyar shi. Ba ta san me yasa ba, komai Uncle ya yi burge ta yake koda kuwa ace fada ne yake mata. Ta sha tambayar kanta, anya za a samu mutum mai kirkin Junaidu? Ta taba ce da Nabilah matar duk da Uncle ya aura ta caba. Nabilah ta ce "Dalili?" Sai ta dauko mata littafin da ke boye a bayanta, GENDER STUDIES (wani bangare ne na sociology mai banbance jinsin maza da mata). Shafin da aka fasalta halittar maza masu gamsar da diya mace a shimfida, kuma irin mazan da matansu ba sa iya rabuwa da su komi wulakancin da zasu yi masu. Tana jan layi-bayan-layi tana fassarawa Nabilah. Ta kare tana murmushi, ta ce "Edactly Uncle ko?" Nabilah ta kama baki cikin mamaki, ita karance-karancen Maryam ya fara ba ta tsoro. Yadda ta nakalci harshen Turanci ko goyon Birtaniya dole ya sara mata. Ta ce "Ke dai wallahi shegen karance-karancenki sai ya lalataki. Yanzu ina ke ina littafin 'yan jami'a? Tukunna ma ina kika samo shi?" Ta yi dariya cikin nishadi ta ce "A wurin Uncle na dauke rannan daya aikeni in kai mishi littattafi staff-room na ganshi cikin lokarsa shi ma bai sani ba na dauke". Nabilah ta ce "To wallahi ki bar karanta sociology za ki hauka ce". Maryam ta ce "Da Uncle bai hauka ce ba? Ya gaya mini digirinsa ya yi shi ne kan sociology. (With first-class honour) Nima insha Allahu abin da zan karanta kenan". Nabilah ta ce "Sai ki yi azama, me ake da abin da zai juyawa mutum tunaninsa zuwa na Yahudu da Nasara?" Ta ce "Eh, idan kin amince da abin da suke fada ba? Ni dai ina so tunda Uncle shi ya karanta". Nabilah ta kyabe baki ta ce "Kya karaci gulmarki dai, kina son mai abin kina cewa abin kike so". Ta bude baki cikin mamakin Nabilah, ta suri bokiti ta yi waje tana yi mata dariya, tana cewa, "Ku gama kumbiya-kumbiyar taku a yi candy mu zo Galadanchi mu kawo amarya….". Ta bi ta da duka ita kuwa ta falla da gudu. To sai ga shi yau Inna ta fadi wani abu kwatankwacin na Nabilah. Ta yi ajiyar zuciya, ta ce a ranta "Shin ko dai Nabila da Inna gaskiya suka fada ne? I fall in lobe with Uncle Junaidu? Neman tabbacin hakan abu ne mai matukar wahala a kwawalwarta". Ta mike ta fito ganin shiru-shiru Inna ba ta dawo ba daga fita alwala har gari ya waye, gabanta ya soma bugawa da sauri da sauri, cikin matsananciyar faduwar gaba. Ta duba gabas da yamma, kudu da arewa, babu Inna babu alamarta. Ta matsa kofar bayin ta kasa kunne babu motsin Inna. Cikin karfin hali da matsanancin firgici ta ce, "Inna kina ciki ne?" Shiru babu amsa, ta ce "Inna ki yi min gyaran murya idan ba za ki magana ba". Nan ma shiru, sai amsa kuwwar raunanniyar muryarta da ginin kasa ya dauka, ya dawo mata da abinta cikin kunnuwanta. A lokacin ne ta ankara da zanin da ke daure a jikin Inna wanda karfen guga ya makale ya yage. Ba ta son gasgata abin da kwakwalwarta ke son ankarar da ita. Ta matsa ga rijiyar ta leka jikinta babu inda ba ya kyarma. Kafafuwan Inna ta gani a sama, maganar motsi kuwa babu shi a tare da su. Sai ta yiwo waje da gudu tana ihu tana kururuwa a kawo mata agaji, kanta ko kallabi babu, kafarta babu takalmi, hawaye shabe-shabe a idanunta. Abinki da jama'ar kauye, ma'abota hadin kai da taimakon junansu, nan da nan gidan ya cika makil da dan Adam, makotansu da abokan arziki kowa yana ta Allahu Akbar! Hure Allah Sarki!! Nan da nan wasu samari majiya karfi suka hada doguwar igiya suka cilla, biyu suka kama hancin suka rike, daya ya bi ya dauko Hure suka fiddo su. Mairo ta daga ido ta ga wai yau Innarta ce wannan babu numfashi, ta tafi har abada ta barta. Innan da ta rage mata a duk fadin duniya, ita ma ta tafi. Sai ta fadi, wuni guda cur ba tasan inda kanta yake ba. *** F arkawa ta yi ta samu kanta a gidan makociyarsu Karime. A lokacin har an yi wa Innar sallah, an kai ta makwancinta. Mairo ta ja jiki ta takure wuri guda sai a lokacin kuka ya zo mata. Ta yi ta kuka kamar ranta zai fita. Karime na ba ta baki tana rarrashinta. Ta ce, "Wannan ba shi ne karshen rayuwarki ba Mairo. 'Ya'ya nawa ne iyayensu suka mutu tun a wurin haihuwarsu, kuma sun rayu? Ki godewa Allah da Ya nufe ki da tashi tare da su, kika san dadinsu. Ni kin ganni nan ban taba sanin uwata da ubana ba, cikina da wata biyar Babana ya rasu, lokacin haihuwata uwata ta rasu, amma gani nan da nawa 'ya'yan goma sha uku. Ina yi miki ta'aziyya Allah Ya jikan Hure, mutumiyar kirki, mai alheri". Mairo ba ta fasa kukanta ba, addu'a ta ke Allah Ya dauki ranta ita ma ta huta, maraici na uwa da uba ba karamin abu ba ne. Tunaninta shi ne, ina zata kuma samun mai kaunarta a duniya kamar iyayenta? Ina zata je? Da wa zata zauna? Mene ne amfanin sauran rayuwarta? Ba ta da kowa ba ta da komi sai Allah, domin ta fidda lissafin Habibu a zuciyarta. Ta samu kanta cikin kullatar Yaya Habibu, kullata mai tsanani. Ba ta ga ranar da haihuwarsa tai wa iyayensu ba. Karime ta shigo da dambun masara a kwano da ruwa a kofi, ta sa ta gaba lallai sai ta ci. Ta dauki loma ta kai bakinta tamkar mai taunar madaci, haka ta ke taunar abincin. Ta tsame hannunta tana sharce wasu dunkulallun hawaye da suka zubo mata. A lokacin ta tuna babban kuskurenta a rayuwa, ba ta yi wa Inna addu'a ba. Ta mike ta je ta dauro alwala ta zo waje mai tsabta a dakin Karime ta shimfida sallaya, ta suturce jikinta ta tayar da sallah. Tana sallah hawayenta ba su bar ambaliya ba. Da ta idar ta bude Alkur'ani mai Tsarki ta shiga karantawa Inna suratul Yasin da suratul Rahman ta rufe da (du'a'ul mutawaffa) tana addu'ar Ubangiji Ya yi mata masauki da aljannah. Ranar kwana uku da rasuwar Inna Hure ta tattaro duk ajiyarta kudin mota kawai ta barwa kanta, ta ba wa Karime aka yiwa Inna sadakar gumba, waina da kosai. Mijin Karime da Dagacin Gurin-Gawa suka zo suka same ta har dakin Karime suka fara da yi mata ta'aziyyah, sanan Dagaci ya ce sun zo ne su kai ta gidan kanin mahaifinta su damkata a hannunsa, wannan ita ce amanar da za su sauke. Hankalin Mairo ya tashi, zancen Inna ya dawo mata sabo tar! A kwanyarta, "Wata kila abin da nake gudu ne dole sai ya faru... Zaman Mairo da iyalan Abbas". Ta sunkuyar da kai tana kuka, ta ki ba su amsa, Malam Tanimu ya ce "Hakuri za ki yi Mairo, mutuwa riga ce akan kowa, tafiyarki birni ya zama dole, domin ba ki da wanda ya fi shi. Sannan Abbas mutum ne mai ZUMUNCI ki dubi yadda ya rayu yana kyautatawa mahaifinki. Ina da yakinin zai rike ki da amana tamkar mahaifinki, har zuwa sanda zai miki aure". Sai ta mike cikin karfin zuciya, ta yafa mayafinta ta sa takalminta. Karime ta rakata gidansu tana hada kayanta tana kuka. Ta tattara zannuwan Inna da kayayyakinta ta sa a wata tsohuwar akwatun karfe ta rufe, ta tura karkashin gadon bononta. Ta tattara 'yan kudaden Innar irin wanda Junaidu ke ba ta ne a duk zuwan da ya yi, da kudin motar da ta warewa kanta duka ta zuba cikin jakarta ta makaranta. Suka fito Karime ta datse dakin da kwado, tana tafe tana waiwayen dakunansu da madafinsu da ta ke jin tana yi masu kallon karshe ne, wasu hawayen suka zubo. Tana bayan motar Dagaci wata (mitsubishi) mai hayaniyar tsiya, in banda karar injina da salansa ba abin da kake ji, shi da Malam Tanimu suna gaba. Ta kama jikinta tsan-tsan sabida gwaruwar da kanta ke yi da jikin motar sabida rashin kyawun birjin Gurin Gawa. Shi da Malam Tanimu suna ta hirarsu ba abin da ya dame su, ita kuwa sake-saken da ta ke yi cikin ranta na abin da zata je ta tarar a gidan Baffanta da 'ya'yansa marasa adadi da rashin tarbiyya ta ke yi. Sai da suka hau titin gidan zoo sosai sannan motar ta daidaita, tafi-tafi har suka iso gidan Sarki suka billa Yakasai ta nan. Kugin karshe da kwarababbiyar motar ta yi a kofar gidan Alhaji Abbas Maigoro ne. Gida ne ginin siminti mai dakali hagu da dama da manyan zaure irin ginin masu kudin da. Yara kanana da samari suna ta shige da ficen su. Gabanta ne ya soma dukan uku-uku sabida haka ta yi hamzarin jan Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un har ta samu bugun zuciyarta ya yi dai-dai. Suka ce ta shiga cikin gidan ta turo musu Alhajin suka fito kan dakalin gidan suka zauna. Cikin sanyin jiki Mairo ta fito tana tafe tamkar macijiya sulu-sulu abin tausayi. Ta yi sallama a tsakar gidan, Uwargidan Hajiya Habiba ta amsa, wadda ke tukin tuwon dare a bakin murhu. Ta karasa inda ta ke ta tsugunna tana gaishe ta cikin nutsuwa. Ta amsa da alama ba ta gane ta ba, ta ce "Yammata daga ina? Ban gane fuskar ba". Ta dukar da kai ta ce, "Gurin-Gawa". Habiba ta kalle ta sosai na 'yan dakikai, nan da nan fara'ar da ke fuskarta ta bace. Ta juya ta ci gaba da tukin tuwonta. Cikin halin ko'in'kula ta ce "Auyo! Ce min zaki yi MAIRON HURE shalelen HURE, sai yau tasan mu mutane ne da ta turo ki ki gaishe mu? Ce nake har jinya kuka yi anan ta tsayin watanni ba ku san hanyar gidanmu ba, sai dai kullum mu tuka mu ba ku? Ince ko yanzun ma ba tasan kin zo ba kada mu moran mata ke?" Mairo ta share hawayen idanunta, ta ce "Tare muke da baki suna zaure, sun ce suna son ganin Alhajin ne". Sai da ta mula ta ce "Ba ya nan, yana kasuwa, amma yana gab da dawowa". Ta taso sumui-sumui ta fito dakalin gidan ta fadawa su Malam Tanimu sakon Hajiyar. Ta ci gaba da tsayuwa a zauren ba ta koma cikin gidan ba. Malam Tanimu ya ce "Bude motar ki kwaso kayanki mana ki shiga da su?" Jikinta ya yi sanyi lakwas ko numfashi da kyar ta ke shaka, ta ce "A'a, mu dai jira Baffan". Dagaci ya yi nazarinta yana taunar goronsa, ya ce "Mairo ki saki jikinki, nan fa gidanku ne, gidan ubanki ne". A ranta ta ce "Kayya Uba guda daya ne, na tabbata na rasa nawa". Suna nan zaune ita kuma tana tsaye daga cikin zauren kusan rabin awa, Ladidi diyar Alhaji Abbas wadda ta ke kusan tsararta ta dawo daga unguwa rike da hannun kanwarta Rahma ta ci kwalliya kamar me? Tana yafe da wani dan gyale mai kama da abin tatar koko, ta daga ido tana kallon Mairo kana ta kyabe baki ta ce "Ah! Yau wace rana?" Ta yi murmushi, ta ce "Ladidi ke nan, kuna lafiya?" Ta sake kyabe bakin (ga alama al'adarta ne yin hakan a duk sanda zata yi magana), wanda kwata-kwata ba ya mata kyau, don ko daya ba ta da kyawun fuska. Ta ce "Gidan namu ne bai ishe ki shiga ba da zaki tsaya a zaure, ko kuwa wani sabon salon gulmar ne Hure ta koya miki, ta ce idan kin zo ki yi mana, don Baba ya ce mun wulakanta ki?" Ta bude baki tana kallonta kawai cikin mamaki, ba ta ce komai ba, ta yi ciki sai ta danne zuciyarta ta bi ta a baya. Suna shiga Habiba ta ce "Ai na dauka tafiya ta yi babu sallama, saboda uban nata ba ya nan". Ta sake kyabe baki, ta ce "Can soro na ganta a tsaye, salon ta ja mana magana wajen Baba". Amarya Aunty Hajara ta yane labulenta jin cece kucensu, ta ce "Wa nake gani kamar 'yar gidan Hure?" Habiba ta ce "Ke ma dai kya fada, ai ni na dauka batan kai ta yo". Hajara ta saki labulenta tana cewa, "Allah Sarki! Alhajin yana kan hanya don nasan dai ba wajenmu kika zo ba". Mairo dai na tsaye tamkar mutum-mutumi. Tana mamakin rashin mutumci irin na matan Alhaji Abbas. Babban mamakinta daga Habiba har Hajara babu wadda ta ce ta shigo daki. Haka Ladidi ta shige dakinsu na 'yammata ba ta kara bi ta kan Mairo ba. Ta ci gaba da tsayuwa sororo! Wannan yaro ya shiga, wannan ya fita duk ba su santa ba. Wannan ita ce rayuwar da Innarta ta ke guje mata ke nan ta matan birni marasa karah da rayuwar kowa yai ta kansa, ko kuwa abin nan da Bahaushe ke cewa, kowa tasa ta fishshe shi. 7/29/21, 10:05 PM - Kawata: 0989 Ta dago idanunta jage-jage da hawaye, don ganin ko wane ne wannan? Da haka kawai zai zo ya dafata? Ko ta ce da wani tana neman taimako ne? Wa za ta gani? Yaya Habibu ne! Cikin matsanancin mamaki ya ce, "Mairo?" Ba ta amsa ba, illa ta bi shi da kallo, da jajayen, idanunta. Ya sake cewa "Me ya kawo ki nan? Ina za ki je?" Nan ma shiru ta yi masa, sai kallonsa ta ke kamar ta rufe shi da duka don haushi. Ya ishe ta da tambaya, ya barta ta ji da kukan zuci, da takaicin da ya dame ta. Don ji take kamar Amiru ya bula mata kura, ya ja motar rayuwarshi, ya barta. A nashi bangaren, shima Habibun, haushi ne ya kama shi, ya ce "Kina ji ina magana kin yi kunnen uwar shegu da ni? Na ce me ya kawo ki nan, kuma gurin wa kika zo? Ina zaki je?" Nan ma shiru ta yi masa, kamar da dutse yake magana, kuma ba ta dauke idanunta daga kanshi ba. Ta kafe shi dasu kurrrrr! Kamar shi ne ya kori Amirun. Iyakar fusata Habibu ya fusata, ya fizgi hannunta suka fito harabar adana motoci na airport din, yana baza ido don gano inda ta yi fakin. Daga can ya hango motar ta yi mata wani banzan fakin a inda aka rubuta no parking, Security ne cikin fararen kayan ma'ikatan gurin tsaye jikin motar, wato sun kamata. Ya yi tsaki, tsut…, suka doshi wajen, har yanzu yana rike da hannunta, sai janta yake kamar kayan wanki. Ya mika hannu ya zare makullin ya soma ba su hakuri ya nuna musu Mairo ya ce ga dukkan alamu ba cikin nutsuwarta ta ke ba, su yi mishi uzuri su ba shi motar. Abinka da malam bature da bai san cin hanci da rashawa ba, gami da bin ka'ida da dokar duk da aka shimfida masa, kememe sun ki yarda, sun dage dole su dangana da ofishinsu in har suna son motar su, don a ka'ida mai matsala a kwakwalwa, ba a yarda ya tuka abin hawa ba, ya ce lafiyarta kalau, tension ne kawai, suka ce idan haka ne ke nan tana sane ta karya musu doka? Don haka dole su dangana da ofishinsu, amma ba zasu bada motar ba. Cikin matsanancin fushi, Habibu ya dubi Mairo "Kin kyauta, kin ga abin da kika jawo min ko? Yau shekaruna goma cur cikin kasar America, ban taba zuwa ofishin 'yan sanda ba, don haka sai ki bi su ku je, ki yi musu bayanin dalilinki na karya dokarsu, tunda ni kin yi min banza, sai ki je ku karata.......” Ya cika hannunta zai tafi, ta riko bayan rigarsa tana kuka. Ya ce "Wallahi bazan je ofishin 'yan sanda ba, sai dai ki hakura da motar, ki bar musu mu tafi, kuma wallahi-wallahi ba zan sake siyan wata ba". Ta ce ta yarda, don haka suka bar motar a nan, suka nufi motar Habibun. Allah Sarki, dan uwa rabin jiki! Sun yi nisa sosai danja ta tsaida su, ya saci kallon Mairo da ke kujerar gefensa, ya ga har yanzu kuka ta ke mara sauti, ta rufe fuska da mayafinta. Sai ya hadiye fushinsa, ya soma lallashinta cikin dabara. "Ni dai idan don na tambaye ki inda za ki ne kike min wannan kukan, to ki yi hakuri. Mantawa na yi, ashe fa Amiru ya fada min ba kya son tambaya. Ban da abinki Mairo, idan wajen Junaid kike son zuwa, jirgi ya tashi ya barki, ai sai ki fada mini, na yi miki booking din wani, amma ba ki sunkuya cikin dubban mutane kina rafka kuka ba, kamar wata mai tabin hankali. Yana ina Junaid din? Nigeria ko Russia?" Cikin kuka ta ce "Ni fa tunda na yi maka wancan alkawarin, ban sake tuna zancen Uncle Junaid ba". Ya ce "To ina za ki? Ko AMIRU kika biyo?" Hantar cikinta ta karta, ta rasa me zata ce masa, don haka ta ja bakinta ta yi shiru. Habibu ya kuta ya ce "Hakan da kike yi, kina ganin mutumci za ki sayawa kanki? Shi wancan bai ce yana sonki ba, sabida neman gindin zama kika kwashi jiki kika je gidansu don rashin hankali da rashin mafadi. Shi wannan da ya ce yana sonki, kin ce ba kya sonshi, sabida kar ki ci amanar wanda bai ce yana sonki ba. Ya hakura ya bar miki kasar ma baki daya ba garin ba. To uban me kika biyo shi ki mishi? Da kin same shin me za ki ce masa? Yi hakuri na tuba, ka zo ka aure ni ko me? To ni bana son rashin hankali da rashin mutunta kai, aikin zubar da kima, da wulakanta kai. Kin riga kin ce ba kya sonshi, to a barshi a hakan. Allah Ya kawo miki wanda kike so. Don wanda ya ce ba ya sonka tun farko, daga baya ya dawo ya ce yana sonka, to akwai dalilinshi na yin hakan. Wato za ki yi A RASHIN UWA... akan yi UWAR DAKI...? To ba da abokina ba! Idan auren kike so ki yi, ki je ki nemo Junaidun, tunda ba kya son karatun da nake sonki da shi. Abu na dan lokaci kalilan, ba zaki maida hankali akai ba, mazan nan da kike gani, dukkansu matsala ne, shi kansa auren idan ba a tsaya anyi shi cikin nutsuwa ba, babu inda ya ke zuwa. Don haka yarinya, kama kanki. Wayar ma daga yau ba zaki sake rikewa ba, kamar yadda babu ke babu tukin mota. To kin ji". Dai-dai lokacin da ya yi fakin a harabar gidansu, ya juya bayan motar ya dauko falmaran din suit' dinshi da wayoyinshi ya fito, ita ma ta fita, ba tare da ta yarda sun kara hada ido ba. Dina ta tari mijinta kamar yadda ta saba a kullum, amma ya sakar mata harara. Ya fincike jikinsa daga jikinta ya juya ya kara hararar Mairon da ke shigowa sumui-sumui kai a kasa, kamar wata munafuka, ya dawo da dubansa ga Dina. "Da saninki Mairo ta dauki mota ta tafi airport?" Dina ta yi shiru, ya ce "Magana nake, ko ke ma sullutun za ki mayar da ni ku barni na yi ta magana ni kadai?" Ta ce "To me ya faru?" "Ya zan tambaye ki kema ki tambaye ni? Amsa nake son ji kawai, kina sane ta tafi ko a'ah? Yanzu na je kai Amiru zai tashi zuwa Najeriya na ganta tana kuka akan titi uban me ta je yi?" Dina ta hau kame-kame ganin yadda ya hasala sosai, ta ce "Am... Eh, ai sako zata kai wa Amirun". A fusace ya ce "Sakon me?" Ta ce "Ka ga Allah ban sani ba, can tsakaninsu". Ya yi dogon tsaki, ji kake 'tsiiittt!' Ya maida kallonshi ga Mairo "Ba ni wayarki". Ta soma dube-dube a falon inda ta cillar da ita, can ta ganota bayan room heater, ta dauko ta mika mishi. Ya kashe ta gaba daya ya jefa a aljihun wandonsa da sassarfa ya nufi bangarenshi ya barsu nan tsaye cirko-cirko kamar an dasa su a wurin. Dina ba ta yi gigin binsa ba, don tasan halin kayanta sarai, idan ya yi fushi yana bukatar a daga mishi kafa, har sai ya sauko don kansa, wanda ba ya daukar dogon lokaci yake yin hakan. Ba ya son aje ana wani lallashin shi ko ace za a ba shi hakuri. Ta kama hannun Mairo suka nufi dakin Mairon suka zauna a bakin gado. Ta ce "Kin same shi?" Ta girgiza kai, wasu hawayen suka zubo. Dina ta sa yatsunta tana share mata, "Kada ki yi kuka Mairo, mika dukkan lamurranki ga Allah. Amiru yana sonki, na kuma tabbata zai dawo. Shi ma Junaid yana sonki, ina tabbatar miki da shi ma akwai ranar da zai zo. Allah kadai Ya san mijin ki a cikinsu, don haka ki dukufa ga neman ZABIN ALLAH ba zabin zuciyarki ba". Don haka Mairo ta tattara shawarwarin iyayen rikonta, wato masoyan nan nata guda biyu, da ba ta da ya su a duniya: Yaya Habibu, da Maidakinsa, Dina. Ta karbi shawarwarin su da hannu bibbiyu, ta fuskanci jarrabawar karshen shekara da ta tunkarota, wadda daga ita zata shiga shekara ta uku, kuma ta karshe da zata hada digiri dinta. *** A yau suna da tutorial class, kan wani kwas da zasu fara jarrabawa a kanshi. Mairo ta fi duk 'yan ajin su fahimtar wannan darasin, don haka suka bukaceta da ta yi musu karin bayani. Maryam Muhammad Bedi, ta fito gaban ajinsu ta tsaya rike da takardu, domin wani abu ne da ta kware a kai, wanda Uncle Junaid ya koyar da ita, wato dabarun speech in public, ba tare da jin ko da dar a zuciyarta ba. Ta soma feso sassanyan Turanci daga makogaro zuwa harshe, sannan siraran labbanta su furta. Kai ka ce diya ce ga Herbert Spencer. Tana bayani ne akan Segmund Freud's stages of psycho-sexual development, tana farke theory tana yin kaca-kaca da ita tun daga phallic-stage... Anal stage... da 'yan uwansu. Sannan ta koma kan SOCIAL CLASSES; the BOURGEOISIE and the PROLETARIAT………. !!! Habibu da ke cikin 'yan ajin ya sanya mask (fuska) sai ya soma kuka. Sannan ya taso ya fito, zuciyarshi cike da alhinin ina ma ace... Malam Muhammad Bedi, zai dawo duniya yau ya ga Mairon shi na koyar da turawa, da sauran jinsin al'umma. Don haka Mairo yau da ta dawo gida ta ga sauyi sosai daga Yayan nata. Domin dai ya tabbatar ta tsaida hankalinta tana karatun, kamar yadda yake so. Yaje makarantar ne ya shiga cikin ‘yan ajinsu don yayi supervising hakan. Shi da Dina ne cikin three seater suna aiki cikin takardu da kwamfuta. Ya daga kai ya dube ta yana murmushi, a lokacin da tayi sallama ta shigo. "Mairo 'yan makaranta......Mairon Dina….. Mairon Yaya Habibu". Ta yi murmushi, har kumatun ya lotsa. Za ta wuce cikin daki ya ce. "Zo zauna, mota zan sake miki". Da hanzari ta dago ta dube shi. Ya daga mata gira (in affirmation) watau cikin tabbatarwa "Gaya min duk irin motar da kike so ni kuma na yi alkawarin zan yi kaffara in saya miki. Sannan ki mai da walwalarki kamar da, bana son ganin wannan shiru-shirun da kika koma. Sannan Dina ta fada min ko hira kin daina yi da ita, kullum sai karatu. A dinga rage karatun, a dinga baiwa zuciya da kwakwalwa dama su huta, sai karatun ya fi zaunawa sosai. Zan tafi Nigeria gobe, akwai muhimman al'amura da zamu gabatar ni da Amiru a Abuja, zan yi sati daya, me kike so in kawo miki? Dina ta rubuta min kayan abincinmu na gargajiya su kuka, daddawa, rogo, kubewa da sauransu. Ke kuma fa?" Ta yi murmushi kanta a kasa ta ce, "Ladidi nake son gani". Ya ce "Ai an yi mata aure. Kina ganin zan rabo mace da gidan aurenta ne na kawo ta? Ai mijinta ba zai so ba, ki yi hakuri ki kare karatun gida za mu koma gaba daya. Gobe sai ku je da Dina ki zabo motar da kike so, zan bar komai a hannunta". Ta yi godiya, ta kama hannun Little Mairo suka nufi dakinta. Dina da Habibu suka bita da kallo, dukkansu ba haka suke son ganinta ba. Gaba daya ta sauya, tun ranar da Amiru ya tafi, daga daki sai daki, daga littafi sai littafi na gaggan malaman sociology. Habibu na addu'ar Allah Ya sa ba sociology'n ne ya soma taba mata kwakwalwa ba. Shi yasa tun farko bai so ta zabi wannan kwas din ba, amma ta dage ita nan duniya shi ta ke so, ba don komai ba sai don ta zama Uncle Junaidu. Ita Dina da yake tasan dawan garin, wato Mairo ta soma kamuwa da matsananciyar soyayyar Amiru sai ba ta damu sosai ba. Habibu ya daga Nigeria a washegari, da tsarabar Baffa da iyalinshi rankatakaf! Da aiken Mairo ga Ladidi. Ita da Dina suka shiga gari suka yo cefanen kayan abinci da kayan amfanin gida da ya kare, sannan suka nufi wani kamfanin motocin (General Motors) dake nan cikin Michigan ta zabi mota irin tata ta da, watau GMC Terrain ruwan makuba, suka shirya payment Dina ta biya, ta karbo rasidi da takardun mota aka biyo su da ita gida. Duk a kokarinsa na son farantawa 'yar uwarshi, yana sauka a gidan Baffa ya kira wayar Dina, ko gaisawa ba su yi ba, ya ce ta hada shi da Mairo, ga Ladidi ga Baffa. Farin cikin da Mairo ta samu kanta da jin muryar Baffa da Ladidi ba zai fadu ba. Sun dade suna hira, inda Ladidi ke sanar da ita tsohon ciki ne da ita, ta yi mata fatan sauka lafiya, sannan ta baiwa Dina suka ci gaba da hira ita da Habibu. Washegari Dina ta kira shi don su gaisa, amma wayarshi a kashe, sai ba ta damu ba, ta ci gaba da ayyukan gabanta. Karfe biyu na rana agogonsu na can, ta sake gwadawa ko za ta samu, amma wannan karon ma an sanar da ita wayar a kashe ta ke. Yinin ranar zungur, haka ta yi ta nemansa amma ba ta samu Habib ba. Abu kamar wasa, har kwana uku ba su samu wayar Habibu ba, sannan ita ma idan ta buga ba ta shiga. Hankalinta ya tashi, amma ba ta bari Mairo ta gane ba. A rana ta hudu ne dabara ta zo mata. Ta kira layin Baffa, bayan sun gaisa ta ce, ko yana da labarin Habibu? Sun kasa samunshi a waya. Baffa ya yi gyaran murya ya ce "Tun ranar da ya zo, ya samu sakon cewa amininshi Amiru ba lafiya, don haka ya tafi Abuja wajenshi ban san halin da suke ciki ba". Dina ta yi zugum! Da waya a hannu, tunani iri-iri babu wanda ba ta yi ba. Ba ta fatan ya kasance ciwon Amirun yana da alaka da soyayyar Mairo. Ta sanshi bai iya daukan al'amuran rayuwarshi da wasa ba. Idan ya ce, yes to da gaske yana nufin yes din, babu gudu babu ja da baya, raba shi da abin nan da yake so sai wani babban ikon Allah. Sannan Amiru mai-nasara ne, bai taba sanya abu a gabanshi ya kasa samu ba. Jin motsin fitowar Mairo daga kicin ta yi azamar sauke taguminta ta kakaro murmushi, wanda iyakacinsa fatar bakinta, ta ce "Baffa yana gaishe ki, yanzun nan muka yi waya da shi". Ta aje farantin da ke hannunta akan centre-table, ta ce "Ina amsawa. Ni Yaya Habibu lafiya dai ko? Tun ranar da ya tafi har yau ban kara jin wayar shi ba". Dina ta shirga karya "Am, eh, ya kira kina barci ne shi yasa ban tashe ki ba". Ta ja farfesun kifin da Mairo ta aje mata, ta soma shan romon da cokali. Tana satar kallon Mairo ta wutsiyar idonta. Wadda ta maida hankali ga labaran CNN da Mu'azzam Kanti, ke kwararowa. (Alkawari bayan rai). Amma a zahiri ba sauraronsa ta ke ba, kewar dan uwanta ne ya dame ta, da rashin jin dadin rayuwar ko ta yaya, da ta samu kanta a ciki. Ba ta rasa ci ba, ba ta rasa sha ba, mai kyau kuma mai dadi, amma zuciyarta a kuntace ta ke babu dadi. Tana ji a jikinta wani bakon al'amari mai GIRMA na shirin faruwa da ita, wanda ba zata ce mene ne ko na mene ne ba. Washegari da asuba bayan ta idar da sallah, ta yi azkar din safiya kamar yadda ta saba. Ta yaye labulen dakinta tana kallon yadda snow ta yi musu lullubi. Amma hakan bai hana Bature yin harkokin gabansa ba. Yau ranar ta kasance lahadi, don haka ba zata je makaranta ba, kai kofofi da tagogin gidan ma duk lullube suke da dusar kankara. Room heater da ke aiki a dakin bata taimaka ba ko kankani wajen rage azabtaccen sanyin da ta ke ji ba, wanda idan da sabo, to sun saba. Ta hau kwamfuta don duba emails dinta. Bayan ta yi wa sanyi mugun shiri cikin bakaken coat da bakin wandon jeans mai kauri, hand-socks (safar hannu) da leg-sock (safar kafa) duk bakake wul. Sakonnin suka soma bayyana, inda welcome-screen ke tabbatar mata tana da sabbin sakonni guda goma sha biyar. Ta soma budawa, yawanci duk daga Nabilah suke, tana tambayarta abin da ya samu wayarta ta kasa samunta. Ta mayar mata da amsa cewa, ta yiwa Yaya Habibu laifi ya kwace, sai na Ir’eesh inda ita kuma ta ke sanar da ita cewa akwai test' karfe sha biyu na ranar washegari, wato litinin. Sai na wani dan ajinsu Henry baturen Brussels inda yake sanar da ita ya wuce kasarsu don mamarshi ta rasu. Ta taimaka tayi masa wani assignment, ya neme ta a wayarta bai same ta ba. Ta yi mishi ta'aziyya ta tura, sai wani guda daya da ya yi matukar daukar hankalinta, kasancewar an yi shi ne cikin harshen Hausa, da rubutu in italic, sannan babu sunan wanda ya aiko, sai logo na hular ilmi. Ta soma bin rubutun a gurguje. "Nasarar dan Adam a rayuwa, ana gane ta ne tun daga kuruciyarshi. Mutanen da suka samu kansu cikin gwagwarmayar rayuwa daga yarintarsu zuwa giramansu ba sa karewa haka a banza. Ina da yakinin cewa, kina daya daga cikinsu, ci gaba da kokari har sai kin cimma burinki na zama ‘malamar makaranta’, kada ki bari soyayyar da ke zuciyarki ta zamo barazana ga ci gaban rayuwarki. Dora soyayyarki akan turba ta hankali da tunani, ba don fita daga wani kunci ko matsatsi na rayuwa ba". -mai son ki. Ta karanta ya fi cikin 'ya'yan carbi, amma ba ta fahimci me mai sakon ke son isarwa gare ta ba. Wa ya ce da shi tana cikin soyayya ko cikin matsin rayuwa? Ta yi tsaki mai karfi ta goge sakon daga cikin akwatun adana sakonta, amma ba ta iya ta goge shi daga kwakwalwarta da zuciyarta ba. To haka washegari, mai 'logo' na hular ilmi ya sake turo mata da gajeren sako. "........ Some one misses you!". Abin sai ya koma ba ta haushi, wannan karon ma ta goge ba tare da ta ba da amsa ba. A ganinta ko waye, yana son yi mata yawo da hankali ne. Ta so ta fadawa Dina, amma ganin Dinar kwana biyun nan ba ta cikin walwala sai ta kyale ta. Karfe tara na daren ranar, suna bisa tebir dukkaninsu, har yaran, suna cin abincin dare, daga can kicin Lynder ke ta goge-gogenta. Wayar Habibu ta shigo wayar Dina, kar ku so ku ga mazari a wurin Dina garin rawar jiki ta datse kiran da hannunta. Ya sake kira a karo na biyu, wannan karon Allah Ya ba ta ikon amsawa. Muryarshi ba ta fita sosai, kamar mai fama da mura ya ce "Yaya kuke? Ya Mairo da yaran?" Ta yi ajiyar zuciya ta ce "Duk lafiya muke. Haba Habib? Ka barmu cikin fargaba. Akalla ko mene ne ya faru da kai ka daure ka sanar da ni, sannan ka kulle wayar. Duk kwanakin nan hankalina a tashe ya ke". Ya ce "Ki yi hakuri, bana cikin hayyacina ne, I don't want to lose AMEERU. (bana so in rasa Ameeru). Ki debo passport dinku a dakina, daga gobe zuwa jibi ku nemi jirgi ku taho, ki kai yaran gidan Sultana sabida makaranta, ku taho ke da Mairo". Dina ta kidime "Lafiya? Me ya faru da Amirun?" Bai ba ta amsar ko daya ba, ga dukkan alamu kuka Habibun ke yi kasa-kasa, wanda ba ya so ta jiyo. Hankalinta idan ya yi dubu ya tashi. Ba kankanin abu ke sa Habibu kuka ba. Kada Allah Ya sa abin da ya darsu a zuciyarta yanzun ya zam tabbatacce. 7/29/21, 11:15 PM - Kawata: 666667778888 Ranar Litinin. Tun asuba da Mairo ta tashi ta yi sallah ba ta koma bacci ba, ruwa ta taro a famfo ta yi wanka ta shafa mai, ta sanya uniform dinta ta shirya tsaf ta zauna jiran fitowar Baffa. Ba shi ya fito ba sai karfe takwas dai-dai na safe. Ya yane labulen dakin su Mairo cikin sallama ya ce "Ya ya kin gama kimtsawa mu tafi?" Ta ce "Na gama Baffa tun dazu". Ya sa hannu ya daukar mata katuwar jakar, ita kuma ta dauki karamar suka fito. Ta leka dakin Habiba da Hajara ta yi musu sallama suka amsa duk cikin yanayi daya, wato a yatsine, don ita Habiba ba ta so wannan komawa makarantan na Mairo ba, so ta ke abar musu ita tai ta yi musu bauta, don Ladidi ko za a kashe ta ba zata yi musu bautar da Mairo ta yi musu ba cikin kwanaki ukun da ta yi tare da su ba. Shi kuwa Baffa Allah-Allah yake ya maida Mairo makaranta don ta huta da kwarzabar su. Idan ya tuno daga wannan zangon Mairo ta gama makaranta hankalinsa tashi ya ke. Ya soma tunanin da ta gama makaranta idan ta samu masoyi zai ganganda ya yi mata aure, idan ma ba ta samu ba ko cikin mutanensa ya nemi wani wanda ya yaba da hankalinsa ya ba shi ita, shi dai ta bar gaban su Habiba, sai hankalinshi ya kwanta. Ya bude boot ya zuba kayan, ita ma ta sanya jakar hannunta. Ya bude kofar wajen mai zaman banza ta shiga ta zauna, sannan ya zagaya shi ma ya shiga ya tayar da motar suka mika kan titi. Karfe goma dai-dai suna cikin Minjibir, duk wasu shige da fice na dawowar dalibi Mairo da Baffanta sun kammala cikin dan lokaci. Suka yi sallama da Baffan ya kada kan motarshi ya tafi, ita kuma ta nufi ajinsu. Tun daga nesa ta hango Uncle yana rubutu akan allo, wani irin dadi da farin ciki suka ziyarci zuciyarta. Ji ta yi tamkar Baba da Innanta ne suka dawo. Daga can mazauninsu Nabilah ta hango ta, ta kuwa sheko da gudu ta rungume ta, ba tare da la'akari da cewa akwai malami a cikin ajinsu ba. Ya dakatar da rubutun ya juyo, juyowar da ta ke nufin al'amura da dama a gare su a wannan ranar. Mairo ba ta iya ta hada ido da Uncle ba saboda matsanancin kwarjinin da ya yi mata a yau, shi kuma kokari yake ya kalli cikin kwayar idanunta cike da tuhuma da tarin laifuffukanta gareshi. Ya mannawa Nabilah harara ba shiri ta koma cikin nutsuwarta, kai tsaye Mairo ta wuce wurin zamansu shi kuma ya cigaba da bada darasi cikin wani sabon kuzari da nishadi gami da wani karfin gwiwa da ya same shi duk a lokaci daya. Aka fita break amma ita da Nabilah ba su fita ba, sun nutsa hirar bayan rabo. Nabilah ta ce "Yaya Inna? Kusan kullum sai na yi mafarkinku Mairo, tun bayan rasuwar Baba nake jin tausayin Inna, ina gayawa Mamana da Daddy. Dama idan kika yi sati baki dawo makaranta ba zan bi sawunki ko makaranta ta yi min izini ko ba ta yi ba". Idanun Mairo suka kawo kwallah, ta ce "Innar ma na rasata Nabilah ... Ba ni da kowa a yanzu sai Baffana sai Allah da Ya halicce ni. Na zama marainiya Nabilah, ba uwa ba uba…...."Hawaye suka kece mata, ta dukar da kanta cikin cinyoyinta ta ci gaba da kuka. Nabilah ma sai ta sa kuka, tana tuna Inna da kirkin da ta yi mata. Sun dauki mintuna suna kuka, kamar wasu kananan yara. Ba su san yaushe Uncle ya shigo ba, har ya tsaya a kansu. Ya sanya hannu ya kwankwasa desk din da suke sunkuye. Duk hirarrakin da suke yi ya ji su, ya rasa inda zai sa kansa da tausayin Mairo. Ba kankanin abu ne ke sanya Junaidu kuka ba, amma a yau ya ce Maryama I cannot control my tears……….."Suka dago ido suka dube shi cikin ido, Mairo da Junaid ke kallon juna, irin kallon da ba su taba yi a rayuwarsu ba. Wani muhimmin al'amari na samun muhalli cikin kwayar idanunsu. Nabilah sai ta bude baki, galala! Tana kallonsu, tana cewa cikin ranta "A yau dai, dole Mairo ta yarda Uncle Junaid yana sonta……..". Mairo kwana ta yi ba ta yi barci ba, baya ga dacin mutuwar iyayenta da ya dawo mata sabo fil, sai kuma SOYAYYAR Junaid da ke dawainiyya da zuciyarta, amma ta kasa ganewa, sabida kuruciya da wauta. Ga dai zahiri al'amarin ya sauya, amma ta sanya kafa tana takewa da gan-gan. A ganinta mai Junaid zai ci da 'yar kauye kamarta? Sai dai ta ce zuciyarta na yaudararta, tunda shi din bai furta ba. To ita ma ba zata taba yarda da tunaninta ba. Shirye-shiryen jarrabawar fita ya kankama. A wannan dan tsukin Uncle ya takura musu matuka da karatu, musamman akan lissafi (mathematics) da Ingilishi (English). Burinsa kawai Mairo ta lashe dukkan takardunta. Ta gama makaranta with flying colours', ta samu gurbi a babbar makaranta, ta yi karatun da zata dogara da kanta cikin kowanne hali. Idan hakan ta faru to shi kam Alhamdu lillahi... Ya sauke nauyin alkawarin da ya daukar wa Malam Bedi, sannan ne yake jin zai fallasa mata soyayyar shi, don haka wannan ba lokaci ne da ya dace ya fallasa asirtacciyar soyayyarsa ga Mairo ba. Ya manta masu iya magana sun ce "A BARI YA HUCE... Shi ke kawo da rabon wani. Ba ta da abin da zata ce da Uncle Junaidu sai godiya, domin da taimakonshi da kwarin gwiwar da ta ke samu daga gare shi ne ta zana jarrabawar Jamb, Waec da Neco cikin kwanciyar hankali, tamkar ba jarrabawa ta zana ba, sabida yadda komi ya zo mata da sauki. Sai dai kuma wannan gama jarrabawar na nufin al'amura da dama cikin rayuwarta. Rabuwa da UNCLE JUNAIDU? Wani muhimmin al'amari ne da ke cinta a zuci, da zuciyar ba zata iya jurewa ba, da harshe ba zai iya bayyanawa ba. Ina ma Uncle zai ce yana sonta ya aure ta? Ya rabata da rayuwar maraicin da zata je ta fada a gidan Baffanta? Hawaye suka ciko idanunta. A karo na farko da zuciyarta ta kawo shawarar ta nemi Uncle ta roke shi ya aureta, ya tserar da ita daga rayuwar kunci da zata je ta fada, ko da ba ya sonta. Ta shiga neman Uncle cikin makaranta, lungu-lungu, sako-sako, abun kamar wasa ko mai kama da Uncle babu. Tuni dalibai sun soma tafiya, don duk wacce ta fito daga last paper daukar kayanta ta ke ta tafi, bayan anyi sallama da kawaye da abokan arziki. Tana tsaye nan cikin tashin hankali Nabilah ta iskota, "Ga can Baffanki ya zo daukarki yana ta aike a nemo mishi ke". Hankalinta ya kara tashi da ta tabbatar a yau zata tafi ne, tafiya ta har abada daga Minjibir, ba tare da ta yi sallama da Uncle ba, wani mutum daga cikin mutane biyu da ke ba ta farin ciki da buri (hope) a cikin rayuwarta. Tabbas yau ya sauke nauyin alkawarin da ya yiwa mahaifinta. Ta kammala makaranta cike da kyakkyawan zaton samun nasara. Muhimmin al'amarin da ke dawainiya da zuciyarta akan Uncle, ta ke so ta sauke, amma babu Uncle a cikin Minjibir, babu alamarsa. Sai ta sa fuskarta cikin tafukanta ta soma shesshekar kuka. Nabilah ta rungume ta suka ci gaba da kukan tare, sai dai ita Nabilah ba ta san hakikanin dalilin kukan Mairo ba. Ita kuka ta ke na kewa da rabuwa da Maironta, yayin da Mairo ke kuka na tausayawa rayuwarta. Ta kullaci Uncle mummunar kullata, (irin kullatar data yiwa Habibu) ta tuhume shi da YAUDARA da wasa da rayuwarta. Ba tasan inda za ta ganshi ba, ta gaya mishi shi kadai zuciya da ruhinta ke so. Ya taimake ta ya aure ta koda BA YA SONTA. Shi kadai ne namijin da ta ke jin zata iya aure a rayuwarta. Shi kadai ne ta ke jin zai kula da rayuwarta a bayan idon Baba da Inna. Shi kadai ne ta ke kalla ta ji shi kamar Yaya Habibu. Yau shekaru dai-dai har shidda dai-dai da rana daya zuciyarta ba ta taba hutawa da kaunarshi ba. A da kam ba ta gane ba, amma yanzu ta yarda ta amince da mahaukaciyar soyayyar da ta ke yi wa Uncle Junaidu. A yau da ta yanke shawarar fada masa don su tallafi rayuwar juna ta neme shi ta rasa. ***** K arfe hudu dai-dai na yammacin ranar ta litinin suka iso gida, inda direban su Nabilah da ke biye da su don ya ga gidan ya juya da Nabilah, da alkawarin bayan sati zata zo su je da Mairo gidansu, don ba ta taba zuwa ba. Tun daga soro Mairo ta soma cin karo da kwanuka, da busasshiyar miyar kuka a jiki. Gabanta ya ci gaba da faduwa don ta tabbatar ita da rayuwar farin ciki, sun yi hannun riga ke nan. Ta fado cikin wata sabuwar rayuwa ta MARAICI, wadda Innarta ta ke jiye mata. Ta tabbata Inna tasan rashin kirki na matan Alhaji Abbas shi yasa a lokacin rayuwarta ta ki yarda ta zauna da su. Mai za a yi da hali irin na Hajara da Habiba? Sai Allah Ya kyauta. Karatu dai an kare shi, yanzu zama ne za a yi na din-din-din. Kowacce waina za a toya? To bari mu bi Mairo da iyayen rikon nata mu gani. Habiba na daki lokacin da suka shiga, sai Hajara ce a tsakar gida tana tankaden garin tuwo. Baffa ne a gaba rike da jakar mairo, ita kuma ta biyo bayansa rike da wata jakar. Hajara ta amsa musu sallama fuskarta ba yabo ba fallasa. Bayan haka ba ta kara tofawa ba. Baffa cike da takaici ya ce "Hajara baki ga 'yar taki ba ne, ko sannu da zuwa babu? Ai ba a haka". Ta cira kai ta jefe shi da harara, "Cewa za ka yi tashi ki yi tsalle 'yar gaban goshina ta dawo, ba sannu da zuwa ba". Jin cece-kucensu sai Habiba ta leko. Ita kam tayi fara'a ta ce "Ah! 'Yan makaranta an dawo? Lale-lale". Ko ba komai ta samu jakar da zata yi ta yi mata bauta. A dakinsu ta cimma Ladidi ta yi dai-dai sai sharar barci ta ke, dakin kaca-kaca ko'ina kayan Ladidi ne a watse, nan pant, can brazier dukun-dukun da su. Ba ta ga inda zata dosana duwawunta ba a dakin, don haka ta aje jaka ta soma tattara mata shirgin waje guda ta gyare dakin tsaf ta share ta kwashe ta zubar. Ta gabatar da sallar azahar da la'asar da suka wuce ta, ta dauko karamin Alkur'aninta ta soma tilawa. Ko aya biyar ba ta yi ba cikin suratul Ma'idah, Hajara ta kwalla mata kira. Ta rufe Alkur'anin ta ajiye mayafi ta fita. Ta nuna mata tulin wanke-wanke ta ce "Kina ganin aiki ya kacame min amma kika tafi kika kule a daki ko uwar me kike? Oho! Maza wanke su yanzun nan cikinsu zan kwashe tuwon dare". Ta ja kujera ta soma wanke-wanken, Hajara ta sake cewa "Ki dinga iza min wutar nan, sallah zan yi". Ta ce "To". Hajara na shiga bayi Habiba ta fito, ta ce "Cika min randar can da ruwa, ga kuma tsummokaraina ba yawa, ki dauraye min su". Ta zube mata tulin atamfofinta a gefe, ta ce "To bari in karisa wa Aunty Hajara wanke-wanken, ta ce tuwo zata kwashe". Habiba ta ce "Inye, wato aikin Hajara ya fi nawa don ni kin raina ni, sabida ina sakar miki fuska?" Ta tsame hannunta daga wanke-wanken zata fara yi mata wankin Hajara ta fito daga bayi ta ce "Au, bar min wanke-wanken za ki yi sabida kina tsoronta? To ba zaki yi wankin ba, sai kin gama mini". Suka soma bala'i a tsakaninsu, Mairo dai tsayawa ta yi kawai tana kallonsu. Baffa ya shigo yana "Kaiconku! Harshenku a matsayinku na matan aure, amma har a makota ana jiyo ku, asararru wadanda ba su san mutumcin kansu da martabar da Allah Ya yi musu na matan aure ba". Ya dubi tulin aikin da suka tilawa Mairo yana salati, ya ce "Habiba waye zai yi miki wannan wankin?" Ta yi shiru, ya ce "Da ke nake magana fa". Ta soma rawar murya amma ba ta fasa tsiwa ba, ta ce "Au... to, kana nufin haka zamu aje gansamemiyar budurwa kamar Mairo sai dai mu tuka mu bata ta ci ta side hannu ta mike a katifa?" Ya ce "Ina almajirin da nake biya yake yi muku wankin?" Cikin rashin gaskiya ta ce "Bai zo ba". Ya ce "To kwashe kayanki maza-maza tun kafin mu sa kafar wando daya da ke, idan ya zo ya yi miki, ko ki tura 'ya'yanki su kirawo shi ya yi miki, amma bazan lamunci wannan rashin arzikin ba. Mairo ba baiwar uwar kowa ba ce a cikinku, wallahi-wallahi bazan yarda ku maidata baiwa ba. Bazan hanata ta taimaka muku da ayyukan gida ba, amma banda wankau da dakau. Ke Ladidi!" Ya kwala mata kira, ta fito a razane, "Zauna nan don ubanki, ku yi wanke-wanken tare ko in kwashe miki hakora yanzun nan". Ta ja kujera ta zauna tana zumbure-zumbure, suka soma wanke-wanken tare. Wannan tsayawa tsayin daka da Alhaji Abbas ke yi akan Mairo da al'amarinta, ya sayo mata matsananciyar kiyayya a gurin iyalansa, sun dauki tsanar duniya sun daurawa marainiyar Allah, daga su har 'ya'yansu, su suyi mata, 'ya'yansu su yi mata, amma ba zasu kwabe su ba. Barin Ladidi da ji ta ke da da hali, da ta cakawa Mairo wuka ta mutu kowa ya huta da bala'in Baffa a kanta. Kwana bakwai kacal da dawowar Mairo daga makaranta, duk ta bi ta kare kamar kudin guzuri, sai karan hanci da idandunan kadai, sabida rashin dadin rai da rashin kwanciyar hankali. Bata taba ganin mutane marasa imani da rashin darajja dan Adam irin Habiba da Hajara ba. Amma a kullum tana yi musu uzuri da yafe musu cikin zuciyarta. Ba kowa ne zai iya rike dan mutum ba a wannan zamanin, tunda dai sun yarda su zauna da ita, to ba zata kasa yi musu biyayya ba iyakar iyawarta. Wata mota kirar Kia-Rio ta yi fakin a kofar gidan Alhaji Abbas, misalin karfe goma dai-dai na safe. Lokacin Alhajin bai kai ga fita kasuwa ba. Nabilah Bebeji, ta fito daga mazaunin direba tana duba agogon hannunta, ta doshi kofar gidan Alhaji Abbas, tana mai addu'ar Allah dai Ya sa Baffan Mairo bai fita ba. Ta yi sallama a tsakar gidan, Habiba ta amsa yayin da ta bi ta da kallon mamaki. Sanye ta ke da atamfa mai karshen tsada shudiya ta karkata dauri mai ban sha'awa kamar nadin inji, a hannunta 'yar matsakaiciyar jaka ce, samfarin Louis Buittion da takalminta marar tudun dunduniya. In ban da kamshin turaren Rasasi (blue-royale) ba abin da ke tashi a jikinta, ta yane jikinta da gyale kalar atamfarta, daure a hannunta agogo ne shudi samfurin polo. Jiki na rawa Habiba ta dauko sabuwar tabarma ta shimfida mata, ta tsugunna har kasa ta gaishe ta, ta gaya mata ta zo wajen Mairo ne. A lokacin Mairon tana bayi tana wanka, cikin bakin-ciki karara Habiba ta yi mata nuni da dakin su Mairo kamar ba ita ce mai yi mata fara'ar da ta ke yi mata ba. Dakin tsaf ya ke, da yake Mairo ba ta wasa da tsaftarsa, sau dubu Ladidi zata bata, sau dubu zata gyara. Ta samu gefen katifar Mairo ta zauna, ta dauki wani littafi na Mairon da Mairon ta aje, da alama shi ta ke karantawa kamin ta shiga wankan na Dynasties the Ashtons (Condition of marriage), ta ce "Maryama na nan da karance-karancenta". Dai-dai lokacin da Mairon ta shigo, kanta na yararin ruwa domin wankan sallah ta yi, zata soma sallah. Ta harari Nabilah ta ce, "karfe taran ke nan?" Ta yi murmushi ta ce "Go-slow ya tare ni, amma ai na yi kokari, ke fa da sai yanzu kika yi wanka, ni tun asuba Momi ta tashe ni wai inyi maza in shirya in dauko mata Mairo ta ganta". Ta yi murmushi, ta ce "Yau dai da yardar Allah zan ga Momi". Ta ce "kwarai kuwa". Mairo na shiryawa Nabilah na kallonta cikin yin tazbihi ga Sarkin halitta da Ya kaga halittar Mairo. "MAIRO MATAR MANYA CE". Nabilah ta ayyana a zuciyarta. Wani irin jiki lukui-lukui kamar mai shiga wankan inji, ga kwantaccen gashi na fulanin usuli, wanda ke kwance lambam akan dogon wuyanta yala-yala da shi kamar ba zai kitsu ba, alhalin ba ta taba shafa masa relader ba koda wasa. Idanuwanta dara-dara, farare kal masu wani irin maiko da sheki (oily-eyes). Kai ita ba ta taba ganin mace mai lafiyayyen kugu da shafaffar mara irin Mairo ba. Kai ka ce idan ta sunkuya karyewa zata yi. Tana sharce kanta ta lura Nabilah kallonta ta ke, ta ce "Ke don Allah wannan kallon fa?" Ta ce "ke din ce, abun kallon ce Mairo, duk mijin da ya aure ki ya caba, ai ban san haka kike da kyau ba sai yau". Ta yi murmushi ta ce "Ni kuma ban taba ganin mai kyau irin naki ba Nabilah". Ta ce "Kayya! Gyara ne kawai Mairo, ina maganar natural beauty ne". Sai Mairo ta ja bakinta ta tsuke, ba ta kara cewa komai ba. Ta kammala shiryawa tsaf cikin atamfarta ta ganin sarki (Ghana wad), wani tausayi ya kama Nabilah, mace har mace, sai dai ba kayan ado, da da suttura ya ya za a ga Mairo? A hakan ma Mairo abin a juyo a kalla ce, ina ga ta samu sutturu da kayan gyara? Sai dai duk yadda ta so ta dinga taimakawa Mairon tun a makaranta Mairon ba ta yarda, cike ta ke da wadatar zuci, kuma cikin godiyar Allah. Mairo ta yi wa Nabilah jagora zuwa dakin Baffa. Ta zube a kasa ta gaishe shi, ya amsa cikin far'a da cewa, "Lafiya kalau Nabilah, an gama karatu sai aure ko, ko kuwa babbar makaranta za ki wuce kamar kawarki?" Ta ce "Eh, makaranta zan wuce". Ya ce "To Allah Ya ba da sa'a". Sannan ta gaya mishi ta zo ta dauki Mairo su je gidansu, iyayenta su ganta. Ya ce "Babu damuwa, don Allah kada Mairo ta kai dare". Suka ce "Insha Allah". Cikin nutsuwa Nabilah ke tuki har suka hau kan titin sakateriyar Audu-Bako, Mairo ta dauka Tarauni suka nufa, sai ta ga Nabilah ta karya akalar motar ta sha round ta hau kan titin state library, ba ta kai karshen titin ba ta yi kwana ta shiga unguwar Ahmadu Bello Way, ta tsaya a harabar gidansu mai lamba dari da biyu (No. 102), suka rufe motar suka karasa cikin gidan. Tun Mairo na mamakin tangama-tangaman falullukan da suke wucewa har ta daina mamaki, sai tazbihi ga Allah Mai azurta wanda ya so. Ba ta taba shiga gida irin wannan ba ko a mafarkinta. Ba su tsaya a ko'ina ba sai a babban falon Momin Nabilah, wadda ta fito tana tafa hannu tana 'Lale da Mairon Nabilah". Ta yi murmushi ta zamo daga cikin kujera tana gayas da Momin, kamin ai haka tuni Nabilah da wata dattijuwa wadda da alama mai aiki ce sun cika gaban Mairo da kayan tande-tande da lashe-lashe irin wadanda ba ta taba ci ba a rayuwarta. Shi ma Daddyn Nabilah ya sauko yana marhaban da Maryam. Ya zauna a cikin su, Mairo duk ta kasa sakewa sabida bakunta da rashin sabo. Saukin kan iyayen Nabilah ya burge ta. Ta tabbatar Nabilah 'yar gata ce ta karshe, ita kadai ce kwallin kwal, a wurin iyayenta. Daddy ya ce da Mairo da zarar takardunsu sun fito ta kawo mishi zai taimaka su samu gurbi a jami'a ita da Nabilah, ta yi godiya sosai. Karfe biyar na yamma Mairo ta yi haramar tafiya. Akwati guda Momi ta shake mata da kayan shafa da dogayen riguna kala-kala, Nabilah ta maidota gida. Tana shigowa idanun Hajara da Habiba akan jakar hannunta. Jikin Habiba har rawa yake, ta bi bayan Mairo tana son ta ji ina Mairo ta samo wannan diyar arzikin, har ga shi ta dawo da galleliyar jaka cike taf da kaya. Har karo suke ita da Hajara wajen shigowa dakin. Habiba ta ce "Bude jakar mu gani, me muka samu?" Hajara kuma ta ce "Wannan bakauyar ta iya bude irin wannan jakar ne? Gafara nan ki gani". Ta jawo jakar ta soma kici-kicin budewa. Ta zazzago duk kayan da ke ciki tana al'ajabi. Habiba ta ce "Ina kika samo wannan diyar arzikin kuma?" Mairo ba ta yi magana ba suka soma kasawa, Habiba ta daga rigar da ta fi kowacce kyau a ciki, ta ce "Wannan zata yi wa Ladidi". Ta sake daga skirt da rigarshi ta ce, "Wannan sai a bar wa Batulu idan ta kara girma zata yi mata dai-dai, ke ki rike wannan din". Ta tura mata wata 'yar yaloluwar rigar barci suka tattara kashi uku bisa hudu na kayan suka yi waje da sauri har suna tuntube tareda karo da juna kada Baffa ya jiyo su suka gudu dakinsu. Mairo ta ce, "Allah na tuba, suttura tsumma, mene da zan damu kaina?" Duk da Baffa ya hana a bata aikin wahala wanda ya fi karfinta ba su fasa ba a bayan idonsa. Mairo na hakuri da su da kokarin kyautata musu su da 'ya'yansu a kullum, amma ta rasa dalilin da yasa mutanen nan suka ki jininta, ko zata wuni tana aikin bauta, shara, wanke-wanke, wanki da wankin bandaki ba zata taba yi musu gwaninta ba, balle kalmar “madallah” ko “an gode” ta gitta a tsakani. Watanni uku cif da gama makarantar su ta samu labarin fitowar jarrabawarsu, don haka ta soma shirin zuwa gidan su Nabilah don su je makaranta su karbo sakamakonsu. Baffa da kanshi ya kaita gidan su Nabilah tana yi masa kwatance tana nuna masa hanya har suka iso gidan. Ya sauke ta ya juya da cewa, idan sun dawo Nabilar ta maidota gida. Amma Allah sarki, sai ta tarar da Nabilah kwance ba ta jin dadi. Ta zauna a gefen gadon da ta ke kwance ta dora hannu akan goshinta, zafi rau! Momi ta shigo da filet a hannunta mai dauke da soyayyar plaintain da dankali da kwai, ta ce "Ungo ba ta Maryam da kanki, watakila zata ci, tunda ni nayi-nayi ta ki karba". Mairo ta ce "Haba Nabilah, ciwo da rashin cin abinci ai abin ba kyau, ki daure ki ci ko kadan ne don Allah". Ta karba tana kokarin mikewa, Mairo ta tusa mata filo a bayanta don ta ji dadin jingina. Momi ta fita ta bar su. Tana fita Nabilah ta fashe da kuka mai tsanani. Hankalin Mairo ya tashi, ta ce "Lafiya Nabilah? Wani abu ya faru ne?" Cikin kuka ta ce, "Me ye bai faru ba? Hajiyar Daddy ce ta zo ta ce ba ta yarda na ci gaba da karatu ba, aure za a yi min da wani cousin dina. Bayan kuma bana sonsa, kuma sati mai zuwa za a daura auren, shi ma bai ce yana sona ba, wai wata Igbo ya zo musu da ita daga can inda yake karatu a Kudu, shi ne ba su amince masa ba, suka ba shi ni. Allah na tuba auren soyayya ma bai tsira ba a wannan zamanin balle auren tushe? Sabida Allah na yi kama da matar tushen iyaye?" Mairo ta rasa abin da zata ce "Ki ce ba ciwo kike ba, tunanin aure ne. Ni ban ga aibu a nan ba, tunda iyaye ne suka hada, ai ALHERI ne, kuma alherin suke nufin ki da shi. Ki yi biyayya ga iyayenki Nabila za ki ga da kyau a rayuwa. Soyayya aikin banza ce, don watakila yadda kike son mutum shi ba haka ba ne a zuciyarshi ba. Na gani akan kaina Nabilah. Har yanzu kuma ban ga inda soyayya ta kaini ba, sai kunci a zuci, ruhi da gangar jiki. Nabilah yau zan gaya miki abin da ke raina shekara da shekaru. Wato soyayyar Uncle Junaidu. Na dauka yadda na ke azabtuwa a zuci, da gangar jiki da soyayyarsa, shi ma haka yake sona, ashe ni ban sani ba, Uncle ba haka ba ne a zuciyarshi ba. A ranar da na yanke shawarar fallasa mishi asirin zuciyata, a ranar ya zame, ya gudu ya barni, ba tare da ya sanar da ni komi a kanshi ba. Wanda ke nufin ba ya bukatar anymore mu'amala da ni. Har yau ni kadai nasan abin da nake ji a zuciyata Nabilah. Hasashenku ke da Innata, bai zamo gaskiya ba, Uncle Junaidu ba SO NA yake yi ba, tausayina ne da taimako". Nabilah ta yi shiru cikin mamaki, yau Allah Ya nuna mata ranar da Mairo ta bude bakinta da kanta ta fada mata cewar tana son Uncle Junaidu. Ina ma ace shi ma hakan ne a zuciyarshi? Duk duniya ba ta taba ganin mijin da ya dace da Mairo ba, irin Uncle, wanda yasan zahirinta da badininta, jinin jikinsu ke gauraye guri guda yana circulating. Amma ba zata taba yarda cewa wai Junaidu ba son Mairo yake ba. Babu wanda zaka bai wa jinin jikinka sai wanda kake matukar so. Ta dago a hankali ta dubi Mairo ido cikin ido, ta ce "Wallahi Mairo yadda kike son Uncle, shi ma haka yake sonki. Zan yi rantsuwa in dafa Alkur'ani akan hakan. Sai dai ban san dalilinshi na janye kafa a ranar da zaku rabu ba. Zan yi mishi uzuri da wani abu mai muhimmanci a gare shi, amma haka kawai Uncle ba zai ki yi miki sallama ba, sai ko sakamakon wani muhimmin abu da ya faru gare shi. Rashin haduwarku ya zama rahma ke nan ga mutumcinki da martabarki a idanunsa……." Ta yi saurin duban Nabilah, tana mai daga gira ta ce, "Yes, gara da Allah bai baki ikon ki furta masa ba, wai ya aure ki koda ba ya sonki. Duk inda yake, Mairo ni na gaya miki ko ba dade ko bajima WATARANA zai neme ki, ki rike wannan a zuciyarki ki ce, ni na gaya miki". Ta mike ta fada bandaki tana cewa, "Bara na shirya mu tafi, ni har ma na warke da ganinki Mairo". Ta yi dariya, cikin samun nutsuwa a zuciyarta da kalaman Nabilah, ta ce "Dama ba wani ciwo ke damunki ba, sai shagwaba da gata, da suka taru suka lullube ki". 7/30/21, 1:01 PM - Kawata: B Sun isa Minjibir ana sallar azahar, zuwan da ya tuna musu da dabdalar kuruciyarsu. Shekaru shida cur, cikin dalibtaka da al'amura masu dama, da suka faru cikin rayuwarsu, suka tuno Kausar suka yi mata addu'a. Suka karasa Edam office suka amso sakamakonsu. Ba abin da suka fadi, sun cinye sun lashe 9 credits ris. Ina ma Uncle na nan, ya zo ya ga girbin abin da ya shuka? Nabilah ta kasa daurewa ta tambayi Mr. Kayode malamin lissafinsu, ko ina Uncle Junaidu? Cike da alhini ya ke sanar da ita cewa, "Yau watanninsa uku kenan da tafiya karo karatu (in-serbice) zuwa kasar Russia (Ukhrain). Yana daga cikin malaman da federal ta dauki nauyin karo karatunsu a kasashen duniya talatin da biyar". Mairo ta samu wani kututturen bishiya ta zauna ta yi kukanta mai isarta, kuka irin wanda ba ta taba yi ba a rayuwarta, ko a rashin iyayenta kuwa. Ta tabbatar wani bigiren nata ya kuma faduwa. Ta dubi takardunta, wahalar shekaru shidda da Uncle ya yi, yau ga shi Allah Ya cika mishi burinsa, amma ashe ba zai gani ba. Kuka ta ke kukan sabo, soyayya da kewa. Ta tabbatar ta rabu da Junaidu ke nan har abada! Ya yi mata nisan da ba zata taba kamo shi ba. ALHERINSA da kyautayinsa masu yawa ne a gareta da ba zata taba mantawa ba. Soyayyarsa da kaunarsa wani abu ne da ba zai taba gushewa daga zuciyarta ba. Shi kadai ta fara so, kuma shi kadai zata ci gaba da so har zuwa karshen rayuwarta, yana sonta ko ba ya sonta. Ta tabbatar ita ke son Uncle, amma shi ba hakan ba ne a zuciyarsa ba, ai yasan inda zai same ta, da yana sonta da ya neme ta. Ciwon kana so ba a sonka, matukar ciwo ne da shi. Ya san ba ta da kowa a duniya a halin yanzu, daga Baffa sai shi, amma ya yi mata haka, ya ki tallafar rayuwarta a dai-dai lokacin da ta fi bukatar tallafinsa. Ta kullaci Uncle Junaidu kullata mai tsanani, irin kullatar da ta yi wa Habibu tare da alkawarta wa ranta yin kokari ta yakice shi daga zuciyarta, ta fuskanci rayuwa ta karbeta a duk yadda ta zo mata.....!!! *** *** B ikin Nabilah bai yi armashi ba, sabida amaryar da angon duk sun ki ba da hadin kai, sai iyaye da 'yan uwa ke ta sha'aninsu cikin farin ciki. Ko yaushe Mairo na tare da Nabilah, don ita kadai ce zata yi mata magana ta ji. Abinci ma sai Mairo ta lallashe ta sannan za ta ci, don wai fushi ta ke da Momi da Daddy. Ranar lahadi aka kai amarya gidanta da ke Nassarawa GRA. Tana kuka, Mairo na yi suka rabu, don wata irin kauna ce shakikiya Allah Ya hada a tsakaninsu. Mairo ta dawo gida, ta kwanta a yagulalliyar katifarsu. Ta runtse idonta tana tunanin al'amuran rayuwa. Yau dai ga Nabilah ta yi aure ta barta, ita kuma ko sai yaushe ne Allah Zai kawo mata nata Mr. Right din? Tunda Uncle ba ya sonta? A zahiri aure ta ke so, ba kuma da kowa ba da UNCLE JUNAIDU. Karatun ya fice mata a rai, tunda babu Junaidu mai karfafawa. Tana daga cikin halittattun mata masu tsananin bukatar da namiji, amma ba da kowa ba, da wanda ruhi, zuciya da gangar jikin su ke so. Haka kawai tunanin unguwar GALADANCHI ta fado mata a rai. Idan har ba kuskure ta yi a tunaninta ba, Uncle ya taba gaya mata shi dan unguwar Galadanchi ne, da ke cikin birnin Kano. To idan ta je Galadanchi ta ce tana neman waye? Alhalin ma an ce Uncle Junaidu yana Russia? Zata je ta nemi gidan su Uncle, iyayenshi da 'yan uwanshi musamman Ilham, wai an ce Gaida mai gaisheka...!' Zumbur ta mike, ta jona ruwa a heater tana jiran ya yi dumi ta yi wanka, sabida sanyin da ake cikin watan Junairu. Daga can gefe Ladidi ta tashi tana yatsina fuska, ba a jima ba kuma ta soma kelaya amai a tsakar dakin. Mairo na yi mata sannu amma ko kallonta ba ta yi ba. Ta gama aman ko kurkure baki babu ta koma ta kwanta. Mairo ta dauko tsintsiya da abin kwashe shara ta soma gyara wajen don tasan idan ta Ladidi ne, to a bar wajen a haka,. Ta dauko tsumma da omo klin ta goge dakin tas! Ta kunna turaren wuta na tsinke. Idan ba ta manta ba wannan aman Ladidi na shidda ke nan cikin kwana uku, amma ko tunanin ta je asibiti ba ta yi. Ta matsa jikinta a hankali, abinki da dan uwa, ta ce, "Ladidi ki shirya na rakaki asibiti mana, ko magani ne a baki, wannan aman ya tsaya?" Ta yi shiru ba ta ce uffan ba, kuma ba ta kalle ta ba, can kuma ko mai ta tuna? Ta ce "Mu je". A gurguje ta yi wankan ta fito, Ladidi ko wanka babu suka fito. Habiba na tsakar gida ta daga ido ta dube su. Wani irin kishi da bakin-ciki ya tushe mata a kahon zucci, ganin irin kyau da kwarjini na musamman a fuskar Mairo tamkar diyar larabawan Turkiya. Ladidi kuwa kamar a rufe ido don muni da rashin tsafta. Ta ce "Ke Ladidi, ina zaki je da wannan mai kama da kabewar?" Ta kyabe baki kamar yadda ya ke a al'adarta, ta ce "Asibiti wai zata kai ni". "Ciwon me kike da za a kai ki asibiti?" Ta sake kyabe bakin ta ce "Wai don ina amai, ko ta gaji da kwashewa ne? Oho!". Ta gallowa Mairo harara ta ce "Kin ga ni bana son kinbibi da son nuna iyawa, waye ba ya amai idan ya ci abin da ranshi bai so ba? Wuce da Allah ki ba ni waje, ke kuma ungo goro ki ci tashin zuciyar zai lafa". Mairo ta koma daki tana jinjina hali irin na Habiba. Karfe biyar na yamma ta ji karar motar Baffa tabbacin ya dawo. Sai da ta ba shi lokaci ya kimtsa sannan ta je dakinsa, ta same shi yana cin abinci ga Hajara da autarta Umma a gefe, ban da harararta ba abin da Hajara ke yi, amma ita ba ta kula ba, tsugunnawa ta yi har kasa ta gaida Baffan, ya amsa cikin walwala, ya ce "Yaya dai Mairo, babu wata matsala ince ko?" Kanta a kasa ta ce "Babu Baffa, ina so in je Galadanchi ne". Bai tambayi wajen wanda zata ba, ya dauko naira dari biyu a aljihunsa ya mika mata, ya ce "Ga shi ayi kudin mota, amma kada ki bari dare ya riske ki waje". Ta ce "Insha Allahu Baffa". Mairo tana tafe tana tunanin rigima irin tata, ya za a yi ta nemi gidansu Uncle alhalin ba tasan komi a kanshi ba? Ace ma ta sani, me zata je ta ce, kuma me zata je ta yi? Wata zuciyar ta ce "Gaida mahaifiyarsa kamar yadda yake gaida naki". Wannan tunani ne mai kyau. Ta fito daga Yakasai zuwa Bakin Rimi, ta tari tasi ta ce "Galadanchi". Ya bude mata kofa ta shiga. Ba a fi minti goma ba ya sauke ta a unguwar Galadanchi. Ta fito ta ba shi dari biyun Baffa ya ba ta canji, ta gangara dai-dai makarantar gidan Galadima ta tsaya nan tana rarraba ido, ta rasa wanda zata tambaya. Daga can gefe wajen masallaci dandazon matasa ne a zaune suna haramar shiga sallar magriba, ba zata iya shiga cikin wadannan samarin ba don haka ta ci gaba da tsayuwa cikin rashin sanin abin yi. Tana nan tsaye wani saurayi ya zo gittawa ta gabanta ta yi mishi sallama, ya juyo ya amsa, ta ce "Don Allah Yayana tambaya nake". Ya ce "Allah Ya sa na sani kanwata". Ta ce "Gidan su Junaid nake tambaya". Ya ce "Junaid? Ya ya sunan maigidan?" "Gaskiya ban sani ba". "Babba ne ko yaro ne?" "Babba ne, don zai girme ka". Ya yi dan tunani "Kwatanta min shi". Nan ta shiga kwatanta mishi, ya ce "Ke ko gidan Justice Atiku kike tambaya?" Kwarai ta taba jin sunan Chief Justice Atiku Galadanchi a bakin Kausar mai rasuwa, (Alkalin-alkalai) na Jihar Kano. Ta ce "Ina jin nan ne". Ya ce "Mu je na nuna miki". Abinka da karamar unguwa, kowa yasan kowa. Ya yi mata nuni da gida ginin manyan 'yan bokon da, mai malalen suminti, dakali biyu sun sa gidan a tsakiya, ko ina a share tas ko tsinke babu. Ta yi wa saurayin godiya ta sa kai zauren gidan. Ashe yadda wajen yake ba haka cikin gidan yake ba, cikin gidan gini ne sosai na zamani, mai ban al'ajabi, sabida yadda aka kwalmada karfe da rodi aka yi irin wannan ginin ba kasafai ake samun irinshi cikin Nijeriya ba. Ko'ina gilashi sai daukar ido yake hatta kofar shiga falon gidan ta gilashi ce. Ta tsaya a kofar falon tana sallama. Wata dattijuwa da alama mai aiki ce, ta fito tana mata kallon rashin sani. Mairo ta tsugunna ta gaishe ta, ta amsa, ta ce "Yammata wa kike nema?" Ta ce "Babar su Ilham". Ta bude mata kofar falon, ta ce "Zauna a nan, Hajiya tana zuwa yanzu". Ba ta zauna a kujerar ba, a kan wani tattausan kilishi da ke tsakiyar dakin ta zauna. Talabijin na ta aiki cikin tasoshin tauraron dan Adam. In banda kamshin turaren wuta na (Bakhour) ba abin da ke tashi a falon, gauraye da ni'imtaccen sanyin na'urar sanyaya daki duk da sanyin da ake fama da shi kuwa. Ta daga kai a hankali zuwa gabas maso kudu na dakin. Tangamemen hoton Uncle Junaidu ya yi mata sallama, yana murmushi. Wata matsananciyar faduwar gaba ta same ta, ta kura mishi ido ba ta ko kyaftawa. Dai-dai lokacin da ta ji muryar Hajiyar tana yi mata sallama. Ta daga kai ta kai dubanta ga mahaifiyar Uncle Junaidu. Nan ta ga inda Junaid ya debo kyau, tsurarsa. Mace ce ma'abociyar zati da kamala gami da gogayya cikin zuzzurfan ilmin boko. A idanunta farin gilashi ne (medicated). A kiyasce zata yi shekaru hamsin. Amma a idaniyarka ba zata fi shekaru talatin da biyar ba. Ta zauna a kujera fuska cike da annuri, Mairo ta duka tana gayas da ita. Ta amsa cikin murmushi ta ce, "Yammata daga ina? Ban gane ki ba". Itama Mairon sai ta rasa abin da zata ce. Wata zuciyar ta ce "Akul! Kika ce danta kika zo nema, wannan ba mutumcin diya mace ba ne. Kin zo ki gaishe ta ne sabida Allah, da kuma soyayyar danta da Allah Ya dasa miki. Amma ba don kamun kafar neman soyayyar ba". Hajiyar ta sa mata ido tana nazarinta, ta rasa inda ta san fuskar. Haka kawai Allah Ya sanya mata kaunar yarinyar a zuciyarta. Duk inda ake neman kyau da nutsuwa, haiba da kamala to wannan yarinyar ta zarce, ga shi da alamunta ilmi ya ratsata ta ko ina. Amma shirun da ta yi mata ya sanya ta diga mata ayar tambaya (kuestion mark?). Ta sake maimaita mata tambayarta "Yammata daga ina kike ban gane ki ba?" A sannan ne Mairo ta cira kai, wasu irin fararen idanu, gauraye da wani irin blue-blue suka haske Hajiyar, ta yi wa Allah sarkin halitta tazbihi, ta tsarkake Shi, ta tsarkake iko da iyawarSa. Cikin sassanyan sautinta ta ce "Na zo wurin Ilham ne". Ta ce "Ke kawarta ce halan? Don na ga kamar nasan fuskarki". Ta ce "Eh". A takaice. Ta ce "To amma kuwa na yi mamaki da ba ta kawo miki katin bikinta ba, an yi bikinta watanni uku da suka wuce. Suna zaune a Wales din kasar Ingila inda mijinta ke karatu". Mairo ta ce "Allah Sarki, Allah Ya yi ba zamu hadu ba". Ta sake juyawa ta dubi hoton Uncle. Ta sake juyowa ta dubi mahaifiyarsa, wata irin soyayya da kauna na sake mamayar zuciyarta. Ba ta ki ta zauna a nan tare da Hajiyar Junaidu ba, tana yi mata bauta, har karshen rayuwarta koda Junaid ba zai aure ta ba. Wannan ita ce kauna ta hakika, wadda ba a samunta a wannan zamanin. Da gaske Junaid ya yi mata nisan da ba tasan ranar da zata kamo shi ba. Tsigar jikinta ya tashi, ganinta ya dushe, wani duhu ya gilma mata ta daina ganin abin da ke gabanta na wucin gadi. Hajiyar ba ta lura ba, don a lokacin hankalinta ya tafi ga amsa kiran wayar da ya shigo mata yanzu-yanzu. Ta mike tana gyara lullubinta ayayinda ta fuskanci da Uncle Hajiyar ke magana. Hajiyar ta yi mata alama da hannu ta jirayeta. Sai da ta gama wayar ta ajiyeta akan centre table, ta ce da Mairo "dan jiraye ni ina zuwa". Ta koma matattakalar da ta fito, jim kadan ta dawo da leda mai tambarin shagon country mall ta mika mata. Mairo ta girgiza kai alamar ba zata karba ba, don tasan ko ta karba rabon su Ladidi ne, dama ace za su gode ne, to a'a, zagi da bakar magana ne zai biyo baya. Hajiyar ta ce "Ni ba babarki ba ce? Ba zan yi miki ihsani ki karba ba?" Ta sake kai dubanta ga Uncle Junaid da ke cikin hoto yana murmushi. Sai ta ga kamar ya turbune mata fuska, cikin rashin jin dadi. Ta maido ga dubanta ga Hajiyar, kallonta ta ke tsakaninta da Allah da matsananciyar kauna cikin kwayar idanunta. Ji ta yi kamar ta kwantar da kai a kafadunta ta yi kukan da ke cin ranta, ta gaya mata matsananciyar kaunar danta da Allah Ya dora mata. Ta ji dumin da Junaid ya ji, a jikin wannan nagartacciyar UWA, ganin hawaye na neman tona mata asiri ta yi hamzarin karba ta ce "Na gode". Har ta kai bakin kofa zata fita, Hajiyar ta kirata jikinta a sanyaye, don daga dukkan alamu akwai abin da ke damun wannan yarinya, ta ce "Har za ki tafi, ba ki gaya min sunanki ba, idan Ilham din ta yi waya in gaya mata". Mairo ta ce "Ki ce mata Maryam ce". "Maryam-Maryam!" Tana ji a bakin su Ilham, amma a wannan karon Allah bai bata ikon ganewa ba. Har yarinyar ta fita, ba ta motsa daga inda ta ke ba, ta dade tana tunanin inda tasan yarinyar. Mai yasa ba ta tambaye ta daga inda ta ke ba? To akan me zata tambaye ta? Don kwaita zo wajen Ilham? Amsar shi ne, don zuciyarta tana sonta. Ta koma falon ta zauna cike da tunani. Sai ana kiran isha'i ta iso gida, Baffa na alwalar sallah a nan kofar gida, ta tube takalminta sannan ta wuce shi, zuciyarta cike da jin haushin dadewar da ta yi. Ya ce "Ban ce kada ki kai dare ba Mairo?" Cikin matsanancin ladabi ta rausayar da kai tace "Ka yi hakuri Baffa, mota ce ban samu da wuri ba". Ya ce "Ni dai duk inda za a je aje ido na ganin ido, amma bana son ayi dare. Idan kin shiga ki turo min Lawan". Ta ce "To". Habiba na kwasar tuwon dare sanda ta shigo, ta dago kai ta dube ta a ranta ta ce, "Kai wannan yarinya da kashin arziki ta ke, kullum ta fita ba ta dawowa haka nan, sai bakin jini har yau babu wanda ya taba sallama da ita, duk kyawun nan nata. Ladidi kuwa kullum idan mutum biyu ba su yi sallama da ita ba, hudu za su yi". Ta dubi Lawan wanda ke bin ledar hannunta da kallo, ta ce "Ka je Baffa na kira". Ya ce "In an ki fa?" Ba ta yi magana ba ta wuce wajen Habiba ta durkusa ta ce "Mama Na dawo, sannunku da aiki". Lawan ya ce "Wani feleke wai 'Baffa', mu 'Baba' mu ke cewa Babanmu, ba wani Baffa ba. Wai mama yarinyar nan ta fara bin maza ne ta ke shigowa gidan nan da manyan ledoji?" Habiba ta ce "Idan ta bi sun ina ruwanka, ko mace ba don namiji aka halicceta ba? Me muka samu ne Mairo? Miko nan in gani". Ta mika mata ledar ta tusa karkashin kujerar da ta ke zaune kada Hajara ta fito ta gani, ta ce sai an raba da ita. Ta dauki tuwon da ta saka mata a wani kwano duk lamba, ta zuba miyar karkashi akai ta mika mata. Ta karba ta wuce daki cike da takaici. Ashe wani takaicin ke jiranta. Tana sanya kai dakin wani mugun karni ya dake ta. Ladidi ta kelaya amai tun daga bakin kofa har bakin katifarsu. Tana kwance a katifa tana barci kamar mushe ba abin da ya dame ta. Ta fita ta dauko tsintsiya da abin kwashewa ta soma aikin aman kamar zuciyarta ta yo waje don bakin ciki. Tuwon da ba ta iya ci ba ke nan sabida karnin da dakin ke yi, haka ta kwana da yunwa. Washegari Ladidi da kanta abin duniya ya ishe ta, ta rarrafa katifar Mairo ta tashe ta, misalin karfe bakwai na safe. Mairo ta bude ido tana kallonta, yawu ya ciko mata baki ta juya bayan kofa ta tsartar ta ce "Zo ki raka ni asibitin don Allah, na kasa gane abin da ke damuna, amma da gaske ba ni da lafiya". Sai Mairon ta ce "Ki fara zuwa ki tambayo mama tukunna, idan ta amince sai na rakaki". Ta ce "Rabu da ita kawai, zo mu fice tana daki". Mairo ta ce "A'ah, ba za a yi haka da ni ba". Ba da son ran Ladidin ba ta fita ta tambayo Habiba za su je asibiti. Habiba ta dubi diyarta ta ce "Bana so ku dinga jerawa ne kada a ga muninki". Ladidin ta kyabe baki, ta ce "Lallai ma Mama, ni ce ma mummunar?" Habiba ta ce "Sai idan ba ku jera da wannan mai kama da aljannun ba". Ladidi ta ce "Ke wannan ya dama, ni da munin nawa dai ai na fi ta farin jini, kin taba jin ko bera ya aiko yana sallama da ita?" Ta ce "Haka kuwa, ku je sai kun dawo". Suna tafe a gefen hanya har asibitin Murtala, Mairo ta yanko mata kati suka hau layi. Suna nan zaune har aka kirasu 7/30/21, 10:24 PM - Kawata: 98 Likitan yana rubuce-rubuce a file lokacin da suka shiga, Mairo ta tsaya ta harde hannuwa a kirji a bakin kofa. Ladidi ta karasa ta zauna a kujerar da marasa lafiya suke zama. Ya gama ya dube ta ta karkashin gilashinsa ya ce "Me ke damunki?" Ta ce "Ina fama da haraswa, zazzabi da ciwon kai mai tsanani, ga wani yawu da yake taruwar min a baki, bana jin dadin bakina". Likitan ya dau abin awonsu ya sanya a hannunta yana sauraro, sannan ya yi rubutu a wata 'yar takarda ya ce, su je laboratory su kawo masa result. Suka fita suka tambayi lab aka nuna musu. Nan aka bai wa Ladidi robar fitsari aka ce ta je toilet ta yi ta kawo. Nan da nan result ya fito suka koma ofishin likita. Ita dai Mairo tunda ta ga an rubuta positibe hankalinta yai matukar tashi. Likitan ya dube su bayan ya duba takardar ya ce da Ladidi, "Ina mijinki?" Ladidi ta ce "Ba ni da aure". Ya kura mata ido na 'yan sakonni ya ce, "Amma you are pragnant,(kinada juna biyu) watanni biyu cif?" Ladidi ta fiddo 'yan idanunta gaba daya suka yi kuru-kuru, wannan bai damu likitan ba ya ci gaba da aikin da ke gabansa bayan ya rubuta mata magani a wata 'yar takarda. Suka fito jikin Mairo har rawa yake, saboda dimuwa da razana, ita kuwa Ladidi in banda kuka ba abin da ta ke, wai likitan sharri yai mata, duk girman kan nan ta sauke shi tana rokon Mairo wai su je wani asibitin a sake dubawa. Mairo ta sa mata ido, ta ce "Wannan asibitin specialist ne, duk Kano daga Aminu Kano sai shi, hakikanin gaskiya suka gaya miki. Don haka ni babu inda zan kuma zuwa". Ta yi shiru hawaye na zubar mata. Ba tausayin Ladidi ta ke ji ba, tausayin Alhaji Abbas ne, bawan Allah, Baffa bai cancanci 'ya'ya irin wadannan ba. Sun kusa Yakasai Ladidi ta ce "Wallahi Mairo duk abin da kike so zan baki, ki rakani a zubar min da cikin, in Baba ya ji wallahi-wallahi kashe ni zai yi". Mairo ta ce "Ni kuwa mai za ki ba ni Ladidi in rakaki a kashe rai? Tukunna ma ni ban san inda ake zubar da ciki ba. Kin bata wayonki! Amma bana tausayinki, Baffa nake tausayawa. Iyakacin tarbiyya da ilmi ya baku, daga boko har na Arabiyyah, ya tsare muku cinku da shanku, da suttura dai-dai karfinshi. Bai cancanci wannan sakayyar daga gare ku ba….." Ta kai gefen mayafinta ta share hawaye, ta fyace majina, ta ce "Ladidi ke kuwa mai ya kai ki ga yin haka? Idan aure kike so mai yasa ba ki tsayar da daya cikin tulin samarin naki kin aura ba? Mai za ki ce da Baffa ranar da ya gane kin yi cikin shege?" Ladidi ta kufula wai Mairo ta ce ta yi cikin shege, ta ce "Kinga malama bana son wani dogon Turanci, idan ba zaki rakani ba ne mu raba hanya, wancan karon ma da aka ce na yi cikin ai nasan inda na je aka kwakule shi. Ko ance da ke kowa ma kidahumi ne, bakauye irinki? Mtsew!!!" Ta yayyaga takardar likitan da takardar maganin, ta ce "Ki je ki gayawa Baffan naki ya yi duk abin da zai yi kada ya barni da rai idan shi ne..........." Mairo ta sanya 'yan yatsu ta toshe kunnenta, ita kuma Ladidi ta tare dan A dai-daita sahu ta shige, ta ce, ya kai ta Sabon Gari. Tana shigowa gida Habiba ta ce "Ina kika baro Ladidin?" Ba tare da ta dubeta ba ta ce "Tana zuwa yanzu". Ta shige dakinsu ta danno kofa. Ta rasa inda zata sa kanta da tausayin Baffa. Ta soma kuka kamar ita ce abin ya faru a kanta. Wani sassanyan kamshi ya doki hancinta, irin wanda ba ta taba ji ba a rayuwarta. Daga nan ta jiyo muryar Baffa yana salati, yana sallamewa. Ta sake saurarawa sosai sai ta ji ya ce "HABIBU? Wa nake gani kamar Habibu?" Tamkar wadda aka cakawa mashi. Ta ji wani kululun bakin ciki ya taso ya soketa a kahon zucci. Amma hakan bai hanata mikewa ta fito ba, don gasgata kunnuwanta. Wani magidanci ne dan kimanin shekaru talatin da takwas, wankan tarwada, mai zarkadeden dogon karan hanci da yalwar idanu farare kal. Da ganin fuskarshi ka ga Malam Bedi, ta wani fannin kuma Alhaji Abbas sak! Yana sanye da kaftan na shadda Getzner kar-kar da ita, baka wul! Dinkin tazarce, sumar kansa a kwance luf baka sidik, kasancewar ba hula a kansa. Da gani babu tambaya, ka ga mutum da ya dama, ya kutsa cikin ilmummuka daban-daban. Wasu kyawawan yara guda uku, maza biyu da mace daya, sai rarraba ido suke na rashin sabo. Mairo dai tana nan rike da labule tana kallonsu, wasu irin hawaye suka zubo mata, ta yi saurin sakin labulen ganin zai juyo sashen da ta ke. Tana ji su Hajara duk suka firfito suna ta karadi da sallallami, ita kuwa ba ta kara lekowa ba. Mai ya dawo da shi cikin rayuwarsu yanzun? Bayan masu bukatarshi sun shude a doron kasa? Mai zai ce, mai zai yi, ya wanke mugun tabon da ya yi mata a zuciyarta? Mairo kuka ta ke tamkar ranta zai fita, ba ta son ganin Habibu ko kadan a rayuwarta. Gara ta bar gidan, kada ace da shi yana da 'yar uwa, mai zai yi mata wanda ALLAH da UNCLE JUNAID ba su yi mata ba? Ta soma harhada kayanta cikin jakarta da sauri-da-sauri, tana yi tana fyace hanci da hawaye duka. Ba ta ankara ba sai ji ta yi Baffa na kwala mata kira daga tsakar gida "Mairo! Mairo!! Ko Mairo ba ta nan ne?" Ta yi bakam, ta ki amsawa, ta jawo hijabinta ta zurma ta sungumi akwatinta ta yo waje, suka ci karo da Baffa a bakin kofa. Ya ce "Zo Mairo, yau ga Habibu Allah Ya dawo mana da shi". Ta sa kuka, ta ce "don Allah Baffa ka bani hanya in wuce, bana son ganinshi, ba abin da ya hada ni da shi. Idan dai zai zauna a gidan nan to ni zan koma wajen Nabilah". Baffa ya ce "Haba Mairo, waye ba ya kuskure? Ki dinga yi wa dan Adam uzuri cikin kowanne hali, uzuri sau saba'in, kafin ki kama shi da laifi. Ki saurare shi ki ji da wacce ya zo, sannan ki yanke mishi hukunci". Da haka ya lallabata suka nufi dakinshi, inda Habibu da su Habiba su ke. Habibu ya hada kai da gwiwa sai kuka ya ke, kamar karamin yaro. Ba kuma kukan komai yake ba, sai kukan jin rasuwar iyayensa daga bakin Habiba. Baffa ya fada su da fada kamar ya rufe su da duka "Ke kam Habiba ba ki ji dadin halinki ba, ko ruwa ba ki barshi ya kurba ba zaki ce Uwa da Uba sun mutu, gatsar, babu sakayawa, babu nuni da daukan hakuri da YAKANAH (Sunan Littafin TAKORI mai zuwa). Ku tashi ku fita ku ba ni waje, iyayen banza, wadanda ban san yaushe za su san Annabi Ya faku ba". Sum-sum-sum suka mike suka fita. Habibu ya dago kai yana kallon Mairo. Kyakkyawar budurwa ‘yar shekara sha takwas, wadda ya tafi ya bari tana shekaru takwas. Ita ma ta kalle shi cikin ido, sai kuma ta dauke kanta. Ta daure fuska sosai. Ya ce "Mairo Yaya Habibun?" Sai ta fada jikinsa ta sa kukan da ke cinta a zucci. Allah Ya riga ya halicci zuciyarta da kaunar Habibu, babu yadda zata yi, shi ne dolenta a rayuwa. Suka rungume juna suka yi ta kuka, Baffa ma tunanin dan uwansa ya dawo masa sabo. Ya soma share ido da habar babbar rigarsa. Sai da suka yi kukansu mai isarsu, sannan Baffan ya soma lallashinsu. Ya ce "Ni ina nan Habibu, zan zame muku uwa, uba, kuma abokin shawara. Dukkaninmu na haka ne, kowa jiran wa'adinsa ya ke". Habibu ya ce "Kaicona Baffa! Dukiyar da na zauna ina tarawa don Baba ya daina noma, Inna ta daina girki da icce, Mairo ta yi karatu mai kyau sun tashi a banza! Na kintata ne zuwa sanda zata gama sakandire sannan in dawo, ashe bazan tadda Baba da Inna ba, sannan Mairon ba ta ji dadin dawowata ba!!" Baffa ya ce "Wai haka Mairo? Ba ki ji dadin dawowarsa ba in sallame shi?" Ta yi murmushi, ta sake sunne kanta a kirjin Yaya Habibun. Ya ja karan hancinta, ya ce "Ko kallon 'ya'yanki ba ki yi ba, balle mai sunanki, mai kama da ke". Sai a lokacin hankalinta ya koma ga yaran. Cikin murmushin kaunarsu da ta mamaye zuciyarta farat daya, ta ce "Ya'yanka ne Yaya Habibu?" Ya gyada mata kai, "Ya'yana ne. Na yi aure da mamarsu tun sanda na kammala karatun digiri na farko. Ga Abbas, ga Muhammad (Bedi), sannan ga Mairo". Baffa ya yi murmushi, ya ce "Taho takwarana". Abbas ya matsa gare shi, dan kimanin shekaru hudu, Muhammad shidda, Mairo kuma 'yar shekara biyu ce. Babban wato Muhammad ya ce "Daddy wannan ne Babanka?" Ya ce "Eh, shi ne Babana". Ya kuma cewa, "Wannan ce Aunty Mairo?" Ya ce "Eh ita ce Aunty Mairo". Ya matso jikin Mairo ya jingina da kafadunta, ita kuma sai kokarin daukar takwararta ta ke, amma ta ki, ta like jikin babanta. Ya ce "Ai ita kiwar tsiya gare ta, wanda yake kulaki ba ki kula shi ba". Ta yi murmushi ta ce "Abbana, Muhammad". Ya yi murmushi ya ce "Anti Mairo za ki je gidanmu?" Ta ce "Insha Allahu". "Za ki yi min tatsuniyya ta gizo da koki irin wadda Daddy ke mana?" Ta ce "A'ah, ni ban iya tatsuniya ba, ni sai dai na karanta maka labarin jaruman maza, irin su Ilya dan mai karfi, da Malukussaif Ibn Ziyyazanun". Ya yi dariya ya ce "Ni kuma zan tuka ki a jirgina (helcopter) wanda Daddy ya sayo min". Ta rungume shi ta ce "To Abbana". Baffa ya ce "Amma Habibu na yi mamaki da ka iya yin wadannan shekarun ba ka waiwayi gida ba, ko gaisuwa ce ai ka aiko mana, idan ba ka zo ba (a lokacin ba kowa ke da wayar hannu ba, sai wane da wane)". Habibu ya ce "Kuskuren da na yi ke nan, amma kusan kullum ba a rasa masu zuwa Najeriya daga Malaysia. To sai dai ita kanta Maleshiyar na dade da barinta, tun bayan da na kammala karatun digirina na farko. Dina abokiyar karatuna ce, diyar Ambassadan Nijeriya a kasar Maleshiya. Mun dade muna soyayya, mahaifinta ya so mu dawo gida ayi auren gaban iyayena, na nuna masa ni ba yanzu zan koma gida ba, ina da babban uzurin da ya rabo ni da gida, idan na koma mawuyaci ne Babana ya barni na dawo. Don haka ya tsaya tsayin daka har muka yi aure. Da taimakon mahaifinta na samu aiki na wucin gadi (temporary) ina yi a wani kamfanin kera takalman fata. Na dade ina aiki a nan kuma na samu alheri yadda ba kwa zato. Daga baya wani abokina Amiru da taimakon mahaifinsa ya yi min hanyar da na samu gurbin karo karatu a Michigan din Amurka, akan kwamfuta da duk abin da ya shafe ta. Ina gamawa ba da jimawa ba na samu aiki a Bankin Barclays reshen kasar Amurka, don haka muka koma can. A can aka haifi Alhaji da Mairo, Muhd ne kadai aka haifa a Kuala-Lampur (Malaysia). To kun ji, don haka bazan dade ba, don wajen aikina suna bukatana, ina so zan tafi da Mairo". Mairo ta yi azamar dago kai ta dube shi, da gaske ya ke ko wasa ya ke? Babu alamun wasa ko kankani a fuskar Habibun. Shi kuma ya kafa mata ido cike da tsoron, kada ta ce ba zata zauna da shi ba. Shi kam nan duniya bai ga abin da zai sake raba shi da 'yar uwarshi ba, wadda ta rage mishi kwal a duniya. Baffa ya ce, "Anya a yi haka? Ni dai na fi so inyi mata aure, hankalina zai fi kwanciya. In lissafina dai-dai ne shekarunta goma sha takwas cif, aure shi ne ya dace da ita". Cikin murmushi Habibu ya ce "Ta fitar da mijin ne?" Ya fadi yana kallon Mairon, ta yi hamzarin sunkuyar da kanta. Baffa ya ce, "A'ah, ita ko zancen nan da samari irin na su Ladidi ba ta yi, idan ka ganta ta fita, to muhimmin abu ne ya fitar da ita. Amma akwai wani abokina Alh. Salisu da ya yi min maganarta tun wancan watan na ce ya dakace ni sai na yi shawara da ita tukunna". Habibu ya ce "Har nawa Mairon ta ke? Ka yi hakuri Baffa ka ba ni ita makaranta zan sa ta, idan ta soma ko ba ta kare ba idan mijin ya fito sai a yi auren, amma Alh. Salisu ai ya yi mata tsufa". Baffa ya ce "Ni ma abin da na yi la'akari dashi kenan, shi yasa ban baiwa zancen wani muhimmanci ba, sai ka yi mata fasfo ku tafi, Allah Ya sa hakan shi ne alkhairinta". Habibu ya ce "Amin". Ya dubi Mairo ya ga ta sunkuyar da kai, ba ta dago ba ya ce "Mairo ko ba kya son zama da ni da 'ya'yanki?" Ta yi murmushi ta ce "Mamarsu zata yarda?" Shi ma ya tayata murmushin, ya ce "Kada ki damu. Dina mace ce mai fahimta, ga kirki da hankali. Na yi mata kyakkyawar shaida. Ta sanki, ta san labarinki ba tun yau ba. Ta fi ni damuwa da a dauko ki, ina gaya mata akwai lokacin da nake jiran isowarsa ga shi Allah Ya kawo". Baffa ya ce "Ita tana ina?" Ya ce "Tana garin Dutsinma, can home town dinsu, gobe insha Allah zan je na dauko ta". Rahma diyar Hajara ta shigo da kular abinci da farantai ta aje ta fita, Mairo ta matso ta zubawa Habibu, ya karba yana cewa, "Yaushe rabona da cin dan wake?" Baffa ya yi dariya ya ce "Ai ga Mairo nan sai ta dinga yi maka dan wake, idan matarka ba ta iya ba". Ya ce, "Tana yi min na fulawa (gudun kurna), amma ba irin shi nake so ba, wannan da ake yi da rogo da kuka shi na fi so, don ya fi sulbi, yafi saukin wucewa a makogaro". Mairo ta zuba filet daya da yaran ta ja su suna ci, Baffa na bai wa Habibu labarin bayan rabo. Habibu ya kammala ya ajiye farantin, ya tsiyayi ruwa a jug ya sha, ya ce "Na zo da ma'aikata Baffa, gobe insha Allahu za a rushe gidannan a yi ginin zamani yadda su Inna Habiba da sauran yara za su fi sakewa". Baffa ya yi murmushi ya ce "Allah Ya ba da iko Habibu". Ya juya ga Mairo ya ce "Je ki share min dakina na zaure, anan zan sauka zuwa gobe, yaran ki kwana da su, ni zan shiga cikin gari wajen tsoffin aminai, gobe idan Allah Ya kaimu sai mu je can immigration maganar fasfo". Ta ce "Ita kuma Anti Dinan a ina zata sauka idan ta zo?" Ya ce "Tana da inda ya fi nan ne? Duk nan zamu sauka". Ta tasa yaran a gaba suka nufi cikin gida. Habiba da Hajara dai duk kunyar Habibu ta ishe su, sakamakon rashin arzikin da suka san suna yi wa Mairo. Ba su taba zaton Habibu zai dawo ba, ga wata irin galleliyar mota da ya iso da ita mai nuni da lallai Habibu ya kama kasa, ga 'ya'ya firda-firda kamar 'ya'yan kajin gidan gona, da gani babu tambaya iyayensu sun gama samun nasibin rayuwa. Habiba ta karbi 'yar daga hannun Mairo, ta sa zani ta goyata, ta ce da Mairo "Ladidi har yanzu shiru, ina kika barota ne?" Ta ce "Tana can asibitin ta ce zata dan jima". Baffa ya fita ya dawo da gyararrun kaji guda goma, ya ce a yi wa Habibu girki. Mairo ta je ta share dakin Habibun da ke soro, ta kunna turaren wuta ta gyare ko'ina. Ta shigar da kayan Habibun, bayan ta ware kayan yaran. Daga Hajara har Habiba sun shiga hankalinsu musamman ganin yadda ake sauke buhunhunan shinkafa, katon-katon na taliya, garewanin mai, katon na juices, na gwangwani da na kwali, buhunan sugar, doya, dankali da sauransu, duk aka jibge musu a store. Ladidi ba ta dawo gidan ba sai dare, wujiga-wujiga da ita, ba wanda ya ga shigowarta sai Mairo don duk sun yi barci, ta lallaba ta kwanta a katifarta, ga dukkan alamu ta je an cire mata cikin. Ladidi sai ta daina bai wa Mairo mamaki, ta koma ba ta tsoro. Washegari ta shirya ta yi wa yaran wanka ta shirya su, Hajara ta ba su abin kari koko ne da kosai da agada, da suka kammala suka tadda Habibu a dakin Baffa suna kalaci shi da Baffan. Yaran suka nufi Babansu suka baibaye shi, ya ce "Ba ku gaida Baffa ba Muhammad". Suka hada baki suka ce, "Baffa ina wuni?" Ya ce "Ina kwana dai takwara na, kamar ba haihuwar Turai ba, Hausa ras a bakinku". Habibu ya ce "Ai ni bana yi musu Turanci, Mamarsu ce ta ke musu. Ita ma ina hanata don kowa yabar gida gida ya barshi". Baffa ya ce "Wannan haka ya ke, Allah Ya raya mana su cikin addinin islam, amin". Suka bar yaran wurin Habiba, suka nufi Immigration office, can hanyar farm center cikin dan lokaci aka yi wa Mairo passport aka ce su dawo bayan kwana uku su karba. A hanyarsu ta dawowa Habibu yana tuki cikin nutsuwa Mairo tasa ido tana kallon shi yana burge ta, ya yi kyau ya yi girma, ya zama ingarman cikakken mutum ma'abocin kwarjini na musamman da cikar zati. Ta fadi a ranta gaskiya wannan Dina ta caba miji. A ranta kuma tana kissima shin ita kuma Dinar yaya zata kasance? Jikinshi ya ba shi Mairo kallonshi ta ke, ya yi wani irin murmushi mai ban sha'awa har fararen hakoranshi suka fito. Ya dan juyo ya ce "Ya ya dai Mairo? Irin wannan kallo haka? Ko na yi kama da saurayinki ne?" Kunya ta kama Mairo, ta rufe fuska tana dariya, "Ni ba ni da wani saurayi. Ka yi kyau ne da yawa Yaya Habibu, ka zama babban mutum mai ban mamaki, don Allah mai Anti Dinar nan take ba ka ne?" Ya yi murmushi ya kai hannun hagunshi ya shafi kwantacciyar sumar kanshi, ya ce "Soyayya ta ke ba ni Mairo. Duk wata kauna ta duniya Dina ta ba ni tun a lokacin da nake dalibi, ba ni da komai, ba ni da ko kwabon da zan aure ta, a matsayina na dan kauye da matsayinta na diyar Ambassador. Habibun kawai ta ke so ba wai wani abu da Habibun ya mallaka ba". Mairo ta ce cikin zuciyarta, "Kamar ni da Uncle Junaidu". Ba tasan cewa furucin ya subuto ya shiga kunnensa ba 7/31/21, 8:31 PM - Kawata: 990 Ya rage gudun motar ya dube ta sosai, hawaye ne fal idanunta "Kika ce mun ba ki da saurayi, Mairo". Ta kai 'yan yatsu ta share hawayen idanunta "Kuka Mairo? Mairo me ya sanya ki kuka?" Ba amsa, karewa ma, sai ta soma shesshekar kukan sosai. Ya sauka gefen titi ya kashe motar. Ya mika hannu ya kama hannunta, ya damke cikin nasa "Daga yau ba zaki sake kuka ba Mairo, tunda ga ni. Babu abinda Allah bai mallaka min ba. Gida a America, gida a Abuja, motocin hawa sai wadda ranki yake so. Ga babban aiki da BARCLAYS BANKS, ga takardun ilmi har zuwa PhD, wanda nake da yakinin daga mu har jikokinmu da 'ya'yan jikokinmu babu mu babu talauci. Jami'a sai wadda kika zaba cikin kasar America. Gaya min wane ne Junaidu? Ni kuwa in aura miki shi ko shi ne beran masallaci sabida talauci, ko shi ne Bill Gates sabida arziki, amma fa sai idan yana da ilmi, ya kuma yi alkawarin zai rike min ke da amana". Mairo ta sunkuyar da kai, ta ce "Ai bai taba cewa yana sona ba!". Habibu ya ce "Ke ce kike sonshi ke nan?" Ta ce "Ni ma ban sani ba ko son nasa nake yi. Alherinsa da kyautayinsa masu yawa ne a gare ni. Ya tsaya tsayin daka akan karatuna, ya tsaya tsayin daka akan lafiyar Baba da Inna, ya ce nima cikakkar mutum ce a lokacin da nake jin kaina cikin inferiority compled. Don haka bazan iya ce maka Uncle Junaidu saurayina ba ne, sai dai duk duniya babu wanda nake jin zan iya aure sai shi…...." Ta shiga baiwa Habibu labarin tun bayan tafiyarsa, yadda akai ta je FGGC, haduwarta da Junaid, Kausar da su Nabilah, saran da maciji ya yi mata, ba da jininsa da ya yi gare ta, karfafa mata gwiwa da kwarin gwiwar da yake ba ta a karatunta, amanar da Malam Bedi ya ba shi a kanta, tsayawa da ya yi akan lafiyar iyayensu, har zuwa gama makaranta da nemansa da ta yi ranar candy ba ta ganshi ba. Ta kare labarinta da ba shi labarin zuwansu karbo sakamakonsu a makarantar inda aka gaya musu ya tafi karo karatu Russia. Ta dakata ta share hawaye, ta cigaba da ba shi labarin zuwanta gidansu wajen mahaifiyarsa, amma ba ta gaya mata ko ita wace ce ba. Habibu ya yi shiru, cikin zuzzurfan tunani na ma'abota hankali. Ya rasa ta inda zai bullowa al'amarin Mairo. Tabbas soyayya ke dawainiya da kanwarshi tilo, ba tareda ita din ta sani ba. Dole ya tsamota, ya ba ta (hope) na yadda zata manta, ta fuskanci sabuwar rayuwar da ke gabanta. Neman Junaid agareshi ba wahala ba ne, zai iya kai ta kasar Russia, to amma ba zai iya cewa da Junaid don Allah ya aureta ba, tunda shi din ba sonta ya ke yi ba. Da yana sonta da ya nemeta, tunda ta ce yasan da Alhaji Abbas. A ganinshi ma, a wannan sabon zamanin da muka shigo. Mairo ta yi kankanta da aure, yana sonta da ilimi mai zurfi ba soyayya ba. To amma shi kansa ya kasa yanke hukuncin cewa Junaidun yana son Mairo ne ko ba ya sonta? Idan ba sonta yake ba haka kawai ba zai yi ta dawainiya da rayuwarta har haka ba. Allah ne kadai Ya san wane ne mijinta. Don haka ya kada harshe ya ce "Za ki yi min wata alfarma, Mairo?" Ta dago a hankali ta dube shi "Ta mece ce Yaya Habibu?" "So nake ki manta da Uncle Junaidu. Ba wai ki manta da alherinsa gare ki ba, a'ah, ki manta da soyayyar da zuciyarki ke yi masa, da tunaninki na ba zaki iya auren kowa ba sai shi. Amma kullum kika yi sallah ki dinga yi masa addu'ar budi da nasarar rayuwa kamar yadda ya zama sanadin da kika samu ingantaccen ilimi. Ni ma zan tayaki, zan dinga yi wa Junaid addu'a, wannan shi ne kawai alherin da za ki yi ki rama mishi, ba lallai sai kin aure shi ba. Da yana sonki da ya zo neman aurenki. Ko bai zo neman aurenki ba, da ya zo ya yi miki sallama a lokacin da zai tafi, ya gaya miki wata kwakkwarar magana, mai nuni da yana son aurenki a nan gaba. Ko ya ce ku yi alkawarin aure, don haka ki manta da soyayyarsa, ki tsaya ki yi karatu irin na Junaidu, ke ma ki taimaki mutane kamar yadda Junaid ya taimake ki. Ki zama malamar makaranta, mai nagarta irin Junaidu. Idan Junaid mijinki ne, wata rana ni na gaya miki zai zo inda ki ke, Allah Zai hada ku, amma hakan ba yana nufin za ki zauna zaman jiransa ba ne, a'ah, matar mutum kabarinsa. Na ji dadi da ba ki gaya wa mahaifiyarsa ko ke wace ce ba, da ina nan ma, da ba zaki je ba, koda yake ba wajenshi kika je ba, wajen wadda ta yi SANADIN kawo shi duniya ne, gaishe ta da zuciya daya ba laifi ba ne. Ita darajar diya mace a wurin da namiji guda daya ce, don haka yi min alkawarin mantawa da soyayyar Uncle Junaidu. Ki bude file ki sanyata a ciki, ki rufe, ki adana. Ki fuskanci rayuwarki ta gaba, kin ji Mairona?" Cikin shesshekar kuka ta ce "Na ji Yaya Habibu, na yi maka alkawari". Ya tayar da motar suka harba kan titi. Mairo na addu'a cikin ranta, Allah Ya ba ta ikon rike wannan muhimmin alkawari da ta yi wa Habibu, domin ba karamin nauyi ba ne ya azawa zuciyarta ba, da ta ke fatan Allah Ya ba ta ikon saukewa. *** *** "KUDI" Aka ce su ne 'KARE MAGANA'. Suna zuwa gida me zata gani? Ma'aikatan Julius Berger. Sun sa katafila sun murkushe gidan Alhaji Abbas, sai fili fetal. Tuni har sun fara auna rodi sun kakkafa matattakalar katako sun fara aikinsu. Su Habiba da yaransu duk suna gidajen iyayensu, sai an gama ginin zasu dawo. Can gidan su Habiba suka je suka dauki yaran, Habibu ya zuba su a mota suka wuce Dutsinma. Mairo da takwararta da Muhammad da ta ke kira Abbana suna baya, Abbas yana gaba tare da Habibu, wanda ke tuki cikin kwarewa da sukuni. Abba yana ta yi mata tambayoyi tana ba shi amsa dai-dai yadda kwakwalwarshi zata dauka. Sanyin A.C gauraye da ni'imtaccen kamshin turaren Yaya Habibu na 'Miyaki' ya gauraye motar. Ya sanyawa Mairo wata irin nutsuwa cikin zuciyarta. Habibu bai tsaya ba sai a garin Funtuwa, ya sai masu gasassun kaji da lemunan kwali da ruwan Faro, suka mika. Bai kara tsayawa ba sai a kofar gidan kakannin matarshi da ke cikin garin na Dutsinma. Habibu ya fidda waya yana kiran Dina, ya ce "Ga mu nan mun iso". Mairo na gefe, harde da hannuwanta a kirji. Idanunta kur, akan kofar fitowa gidan, tana zuba idon ganin wace ce wannan Dina, da ta mamaye zuciyar Habibu haka? Wace ce Allah Subhana Ya yiwa baiwar samun wannan Habibun? 'Yar Katsinawan sai ta fito, kyakkyawar fuskar fal far'a. Sanye da doguwar bakar riga da mayafinta kirar Bahrain. Fara ce, amma ba sol ba, ta ma fi dai-dai da a kirata choculate colour. Mai wadatar giran ido, gashin ido da sumar kai. Ba ta taba ganin mace mai kyawun fata irin matar Habibu ba. Gayun ne ya hadu da jin dadi, ya gauraya da hutu, ya cakude da wadataccen ilmi, sannan kwanciyar hankali da zaman kasar sanyi ya biyo baya. Suka yi wa juna wani irin sassanyar kallo ita da Habibu, sannan ta karaso ta rungume Mairo, tamkar ta tsaga kirjinta ta sanyata don kauna. Wani irin matsiyacin kamshi da Mairo ba ta taba ji ba ya ziyarci hancinta. "Lallai wasu tun a duniya Allah Ya ke ba su Hurul'eeni". Mairo ta ce a zuciyarta. Da tana ganin Dinan ce mai sa'a da ta samu Yaya Habibu, ashe shi ma Habibun mai sa'ar ne, don cikin mata dubu, da kyar zaka samu biyu irin Dina. Da tana ganin Nabilah 'yar gaye, ashe Nabilah 'yar dukununu ce. Ba ta gama zancen zucinta ba, tattausan hannun Dina kamar na jariri ya kama nata, ta ja ta cikin gida. Bayan ta bi 'ya'yanta daya bayan daya da kisses da runguma. Wata dattijuwa ce tsohuwa tukuf, sanye da atamfa super holland zaune a can kuryar kayataccen falon bisa darduma tana lazimi. Da gani babu tambaya, ita ce uwar Baban Dina. Habibu da yaran suka zauna a kujera yayin da Dina da wata yarinya budurwa da alama mai aiki ce suka shiga hidimar fito da warmers, plates, da cokulla. Ba ta katse laziminta ba, shi ma Habibun fita ya yi don samun jam'in sallar la'asar. Mairo tana fashin sallah, don haka suka zauna ita da yaran da Dina suna cin abinci. Dina ta rasa ina taka-saka-ina-taka-aje da Mairo? Soyayyar Habibu ta shafe ta. Ganinta ta ke tamkar kanwarta ta jini. Sai wajejen karfe biyar Habibun ya shigo, lokacin Hajiya ta idar da laziminta, suka soma gaisawa da Habibu. Itama Mairo ta duka tana gaishe ta. Dina ta ja ta dakin da ta sauka, ta hada mata ruwan zafi a baf da turarukan wanka, ta ce ta shiga ta yi wanka. Mairo ta ce, "Ai na yi wanka da safe". Ta yi murmushi, ta ce "Sakewa za ki yi, ita mace so ake ta yi wanka sau uku a rana. Idan hakan bai samu ba, ta yi sau biyu. Sannan na ji smelling din jikinki bai min yadda nake so ba". Don haka Mairo ta hau wanka, cikin kwami da ruwa mai dumi, da kamshin bathrobb din desire-dunhill mai sanyaya zuciya da ni'imtata. Da sabulun da ko a mafarkinta ba ta taba gani ba, wanda in ka yi wanka da shi, ba sai ka shafa mai ba. Ta ji fatarta har wani santsi ta ke da sheki. Jikinta ya yi laushi tubus. Ta dauro alwala ta fito, ta samu Dina na jiranta zaune a bakin gado. Ta zube mata kayan shafa da turarukanta, ta ce ta shafa, sannan ta dauko riga da siket masu kauri na Bersace ta ce ta sanya. Ta zaunar da ita a gabanta ta sa dryer tana busar mata da gashi, sannan ta bi layi bayan layi na gashin ta shafe shi da Indian hemp ta taje ta matse da bound, ta bi jelar ta jere da ribbons kala uku masu taushi. Nan da nan sai ga Mairo ta fito kamar Sushmita Sen. Dina ta yi murmushi ta ce "Maryama, haka kike da kyau kamar Habibu?" Mairo ta ji kunya, ta sunne kanta tana dariya, ta ce "Anti Dina ai ke kin fi Yaya Habibu kyau, fari kawai ya fi ki". Ta ce "Allah Ya nuna min ranar da tawa Mairon, zata girma ta tashi kamar wannan Mairon. Kinga yadda na ganki yanzun nan, haka nake so kullum na ganki. Ita mace ba abin da ya fiye mata jikinta daraja. Idan ta gyara shi, to ta gyara martaba da mutumcinta, mijinta zai like mata tamkar kaska, ya ji ba abin da ya ke so ya kusanta a duniya sai ita. Shi kamshi wata rahma ne da Allah Ya saukar mana mu mata, kuma shi ne babban sirrin rike da namiji. Kin ji ko Mairo?" Mairo na dariya ta ce "To ai ni ba ni da mijin". Ita ma ta tayata dariyar ta ce "Zai zo ne, gallele kuwa, ni na gaya miki". Can dakin baki suka iske Habibu, shi ma ya sake fesa wanka, ya yi shiri cikin T. shirt din DKNY fara sol da ratsin jaja-jaja da wandon jeans kai ka ce saurayi ne dan shekaru ashirin da biyu, babu mai yarda ya aje 'ya'ya uku a duniya, ya bi Mairo da kallo don da fari bai ganeta ba, ya ce "Kai! Halitta!!" Suka kyalkyale da dariya ita da Dina. Ya soma hararar Dinan cikin wata irin soyayyarta da ta kara ratsa zuciyarshi, ya ce "Shikenan kuma don kin yi kanwa ni kin yaye ni?" Ta soma yi masa alama da ido, Mairo na jinsa. Itama Mairon juyawa ta yi ta fice a ranta tana ce, 'Ku cinye kanku da soyayyar". Ai kuwa tana fita ya yi super ya suri Dinan yana cewa "Gaya min wanda ya ce da ke kanwa ta fi miji????" Mairo wajen Hajiyar su Dina ta koma tana goga goro a magoginsu na tsoffi, da gani ka ga 'yar gatan tsohuwa da da ya hucewa takaicin duniya. Ga wasu mulmulallun awarwarayen zinari a hannunta guda uku, sai walwali suke, tufafin jikinta kadai, sun ishi karamin talaka jari. Ta zauna gefenta ta ce "Hajiya kawo goron in goga miki". Ta mika mata dankwalelen goron fari sol da magogin ta soma gogawa, in ya taru ta mika mata ta hambuda a baki. Tana bai wa Mairo labarin Dina. Ta ce "Kin ganta nan, duk cikin jikoki na ashirin da biyar na fi sonta. Sabida halayenta na kwarai da rashin daukar rayuwa da fadi. Babanta shine da na biyar cikin 'ya'ya biyar da na haifa suna mutuwa, shi kadai ya tsaya. Kuma daga shi Allah bai kara ba ni da namiji ba, sai kannensa mata guda biyar. Ita ce 'yarsa ta fari, sai tarin kanne guda bakwai. Ta kawo Yayanki dalibi da ba shi da komai ta ce ita shi ta ke so ta aura. Da fari ba mu yarda ba, tunda ba mu ga iyayenshi ba, shi kuma ya ce, ba zai koma gida a wancan lokacin ba. Ya fito neman ilmi da arziki ne sai Allah Ya yi mishi zai koma, don haka muka saduda muka yi musu aure. Da ya ke abokiyar arzikinshi ce ga shi Allah Ya azurta su, da 'ya'ya da dukiya. Allah Sarki, ashe iyayen da ya nema don su huta, kamar yadda nake hutawa a tsufana, Allah bai yi za su mori arzikinsa ba. Ki saki jikinki, ki kwantar da hankalinki da Dina, zata zame miki uwa, abokiya, kuma Yayar kwarai, kin ji Maryamu?" Ta girgiza kai, ta ce "Na ji Hajiya, Yaya Habibu ma ya gaya mini". Dina da Habibu suka shigo, sun jero, tsawonsu daya, takunsu iri daya, sai annuri ke fita daga fuskokinsu, ga dukkan alamu an ci soyayya an koshi. Ta dubi Hajiya da Mairo da ta takarkare sai nika goro ta ke yi, ta yi dariya ta ce "kawa da kawa, hirar me ake yi?" Hajiya ta ce "Ina ruwanki da hirarmu? Ko mu mun tambaye ki hirar me kika je taya mijinki?" Habibu ya nitse cikin leather yana amsa waya da thuraya dinsa, cikin wani dan bantan uban Turanci kamar Karl Mad sabida yadda Turancinshi ke fita tar-tar irin wanda Mairo ba ta taba ji ba. A da, tana tsammanin a duniya babu wanda ya iya Turanci irin Uncle Junaidu, ashe Junaid rarrafe yake yi, ga wadanda suka mike suke dabo, suka tsaya da kafafunsu. Kwanansu uku a Dutsinma suka tattaro suka yo Kano, Mairo dai kamar ba zata tafi ba sabida jin dadin zama da Hajiya, har hawaye ta ke da suka fito za su tafi, Habibu da Dina na mata dariya. Hajiya ta cika mata Bacco fal da atamfofin edclusibes irin wadanda 'ya'yanta ke kawo mata, don ta dinka, amma ta tattara ta bai wa Mairo. Wannan a jinin Mairon yake, FARIN JINI da shiga zucci. Idan ka zauna da ita yini guda, zaka so ka kwana da ita. Idan ka kwana da ita, zaka so kayi wata tare da ita, idan ka yi wata tare da ita zaka so ka yi zaman shekara da ita, haka idan ka yi shekara da ita, zaka so ka zauna da ita har zuwa karshen rayuwarka. Karfe uku dai-dai na rana suna cikin Kano, Habibu ya karya kan mota suka shigo Yakasai. Tun daga nesa wani dankareren European Billa (Bungalour) ya dauki hankalinta, ya karkada mata 'ya'yan hanji. Abin mamaki a get din gidan Habibu ya sanya hancin motarsa kirar Porsche. Zuciyarta na gaya mata, wai wannan gidan Baffa ne? Amma wani sashen na karyatawa. To idan ba shi ba ne, wanne ne? A nan dai gidan Baffa ya ke, ga makotansu nan ba su motsa daga inda suke ba, su ma sun samu arzikin sabon fenti irin na gidan. Dama dai gidan Baffan babba ne, ga kuma bene an daura, ko ina gilashi da tile ke zagin idonka. An fidda sashen baki daga gaban gidan, a cikin gidan kuma sashe biyu ne na matan gidan, sashe guda na yara, Baffan yana sama, sai dakin 'yammata. Kowanne daki an kafe plasma a sama tana ta aiki cikin tasoshin tauraron dan Adam, ga dindima-dindiman kujeru masu nishi 'yan Italy da labulaye masu garai-garai da gani tafiyayyu ne tun daga China. Abin dai ba a cewa komai sai a gaida Habibu, a gaida ma'aikatan Julius Berger. A gaida Habibu da aikin ZUMUNCI, da rama hairan da hairan. Suna tsayuwa su Rahma suka diba yuuu! Suka yi cikin gida suna ta ihu, “turawan sun dawo da Mairo, ba su sace ta ba. Baba ga Mairon nan sun dawo da ita". Baffa dai baki ya ki rufo, ya fito ya taro su, Abbas ya gane shi, ya je ya kama hannunsa, Hajara da Habiba kowacce ta fito daga bangarenta bakin nan kamar gonar auduga, har rige-rigen daukar Mairo karama su ke. Mairo fa ta fara jin tsoron al'amarin Habibu. Allah dai Ya sa ba kungiyoyin nan na matsafa da sassan jikin mutum ya shiga ba. Allah Sarki! Da tasan Barclays da ba ta ce haka ba. Hankalinta na kan 'yar uwarta Ladidi da halin da ta tafi ta barta a ciki. Don haka suna shigowa ta tambayi Habiba "Ina Ladidi?" Habiba wadda ke jin kamar ta suri Mairo ta goya don ta samu fada wajen Baffa wanda ya daure musu fuska tam ya ki kula su don yasan duk borin kunya suke yi. Ta nuna mata dakin da Ladidi ta ke, ta ce "Halan Mairo a inji matar Habibu ta sakaki ta wanke?" Mairo ta yi murmushi ta ce "A'ah, a lagireto ne". Ta wuce ta barta nan, tana ta sosa keya don kunya. A dakin ta cimma Ladidi, an yi dai-dai cikin Italian bed, ana shan lemon Safari ana kallon tashar Zee-Aflam, ba tasan sanda dariya ta kubuce mata ba, don kwata-kwata ba ta yi matching da gadon ba da dakin gaba daya, ta fi dacewa da mai aikin dakin ba mamallakiyarshi ba. Tana ganin Mairo ji kake kat, ta kware. Ta dinga tari ba kakkautawa. Mairo ta zauna a bakin gadon tana yi mata sannu. Ta mutsittsike ido ta ce "Mairo ke ce kuwa?" Ta ce "A'ah, ba ni ba ce, Ladidi ce". Ladidi ta soma kuka ta ce "Don Allah Mairo ki yafe mini. Ga shi dai tun a gidan duniya mun ga ishara, dan uwa duk lalacewarshi ba abun wasa ba ne, sai dai nasan kome zan fada miki a yanzu ba zaki yarda ba, za ki ce don na ga Habibu ne, ko don abin da ya yi mana, amma wallahi ba haka ba ne. Yadda kuma kika rufa min asiri a duniya, Allah Ya rufa naki duniya da lahira". Ta sa habar zaninta ta share ido. Mairo ta ce "Duk ba wannan ba Ladidi. Ki tuba ga Allah, ki sani cewa, Yana kallonki, idan su Baffa ba sa kallonki. Yau idan Baffa ya samu labarin kin cire ciki har sau biyu a wane yanayi kike tunanin zai tsinci kansa? Idan ba kya tsoron Allah, ai kya ji wa kanki tsoron cututtukan zamanin nan da ba su da magani. Idan aure kike so ki fidda daya daga cikin manemanki ki aura mana?" Ladidi ta ce "Na tuba, na bi Allah na bi ki. Wallahi daga yau bazan sake ba..." "……Ki ma sake din mana don ubanki". Suka juya a razane, Habiba ce tsaye a kansu, ashe ta dade da shigowa ba su ankara da ita ba. Ta kwance dankwalinta ta yi damara, ta yo kan ladidi ta hau ruwan cikinta ta soma kirba mata naushi tana ihu tana "Na tuba Mama, wallahi bazan sake ba". Wannan bai ishi Habiba ba, sauka ta yi ta nufi kicin ta dauko tabarya ta yo kanta tana fadin, "Gara na kashe ki kafin kanjamau ta kashe ki, kibar mana abin fadi cikin zuri'armu". Ganin ta yo kanta da tabaryar Ladidi ta yo waje da gudu don tserar da rayuwarta, wannan ya janyo hankalin kafatanin jama'ar gidan yara da manya, suka fito tsakar gida har Dina da Habibu da Baffa. Ganin Ladidin zata yi waje da rigar bacci, kafarta ko takalmi babu, kanta ko dankwali, Habibu ma ya rufa da gudu ya kamota tana ta kuka, tana "Na tuba wallahi ba zan sake ba…….." Habiba ta fito tana sharar hawaye, ta ce, "Ni fa ince, wannan aman da wannan kwanciyar nakin na Ladidi, ba na lafiya ba ne, na zama shashashar Uwa, yanzu Mairo da kunnawana ba su jiye min ba, haka zaki biye mata ku binne mu?" Mairo na kukan tausayin Ladidi ba ta ce komai ba. Baffa ya ce "Mai Ladidin ta yi ne?" Ya tambaya yana kallon Mairo. Ta yi tsuru-tsuru ba ta yi magana ba. Ya sake tambayarta, ta ki magana. Habiba cikin kuka ta ce "Ciki suka je aka cire mata, wai wannan shi ne na biyu, na ji su tana yi wa Mairon godiyar ta rufa mata asiri". Baffa ya ce "Mairon? Da ita aka je aka cire cikin?" Mairo ta girgiza kai cikin kuka ta ce "Wallahi ba ni na rakata ba, ita kadai ta je abunta. Ni asibiti na kaita ta ga likita". Dariya ta kama Habibu, wai asibiti ta kaita, sai ka ce wata uwarta? Habibu ya ce "Ke ma sai mu je a duba ki, don abokin barawo ai barowo ne". Ya hankada Ladidi da ke hannunsa ya tankado keyar Mairon, ya ce, "Oya! Lets go, har gwajin kanjamau duk za a yi muku tunda kun zama karuwai". Mairo ta soma rantsuwar, wallahi babu ruwanta, ba ta da saurayi, ba ta taba yin zance da namiji ba. Babu wanda ba ta baiwa dariya a wajen ba. Baffa ya kamo hannunta ya ce "Share hawayenki Mairo. Babu inda za ki, kanwarshi ce karuwa ba ke ba". 8/1/21, 9:30 PM - Kawata: Mairo Little Mairo tana ta murnar ganin mamarta da ta kwana biyu ba ta gani ba. Shi kanshi Yaya Habibun idan ka lura zaka ga annurin fuskarshi ya karu sosai. Oh! Ashe haka auren so yake? Mairo ta ce a zuciyarta. Kai ka ce sun shekara ba su ga juna ba. A otel din da Amiru ya sauka (Best Western) suka ajiye shi, da alkawarin sai ya shigo da daddare yin dinner. Kuma Mairo yake so ta yi mishi girki. Dina ta yi murmushi ta ce "Ban fa gane ba, kada ka sa Harrit ta bindige min kanwa". Ya yi murmushi ya ce, "Allah babu wasa cikin maganata Aunty Dina, don ni yanzu kin zama Auntyna, alfarma nake nema ku yi min ke da mijinki, kokon bara na yana gidanku, duk da mijinki is not hundred percently agreed (bai yarda gabadaya ba) sabida wasu hujjojinshi marasa makama. Nasan ke za ki dube ni da idon rahma. Zan ba ku mamaki, zan nemi soyayyar Mairo ba campaign nake so ku yi min ba". Har suka iso gida, Dina na jinjina kalaman Amiru a zuciyarta. Ta sanshi, ta san halinshi kamar yadda tasan mijinta. Karya ko joking ba sa cikin halayyarsa, idan ya ce yes, to da gaske yana nufin yes din babu gudu babu ja da baya. Babu kuma abin da zai sa shi ya janye abin da ya sa gaba. Wani irin mutum ne mai nasara akan duk abin da ya sa gaba, wato dai irin mutanen nan ne masu ra'ayin kansu, ba masu fadin karya don wani ya ji dadi ba. Hakanan ba sa iya boye abin da ke zuciyarsu. Ta dade tana addu'ar zuwan ranar da Allah zai nuna mata mijin Mairo, ta sha kissima yaya mijin Mairo zai kasance? Domin ita din 'yar baiwa ce kamar Habibu. To amma ba ta taba tunanin Amiru ne zai ce yana so ba. Kololuwar ilmi, nasaba, arziki, kyau, nagarta duk shine. Bankin duniya yana hannunsu, kudin Najeriya gaba daya yana hannun ubansa, sai ya rattaba hannu a kansu za a yi amfani da su, ko 'yar shugaban kasa yake so zai aura. Duk kalar macen da yake so da gudu za a ba shi, amma ya ce; MAIRO, a ganinta wannan abin alfahari ne a gare su, ita da Habibu domin Amiru ba zai yi karya ba, ba zai yaudare su ba. Ba zai fadi abinda ba haka yake a zuciyar shi ba. To mai yasa Habib cogewa? Ta san abin da yake gudu ba zai wuce Harrit da 'yammatan Amirun ba, domin iyayenshi mutanen kwarai ne, 'yan jiya, bana yau ba, kuma Habibu kamar Da ne a wajen Abudrrahman Gaya. Da irin wanda ya tsugunna ya haifa. Shi ya dau nauyin karatunshi tun daga master har PhD da sauran kwasa-kwasan da ya halarta. Yasan kuma amintarsu da Amiru ba tun yau ba, don haka ta ke ganin ta wannan fannin ba za a samu matsala ba. Idan ma akwai matsalar ta fannin Harrit ai shi Amirun ba yaro ba ne, yasan yadda zai tsarawa kanshi rayuwa. Suna kicin ita da Mairo lokacin da Amiru ya iso. Dina ba ta ce mata komai ba, sai ta yi ma kamar ba tasan zancen ba. Shi da Raymond ne sakatarenshi, suna hira kan harkokinsu shi da Habibu, amma duk hirar ta gundire shi, sai baza ido yake don ganin ta inda Mairo zata bullo, amma shiru. Habibun na hankalce da shi, yau surukuta sosai yake nunawa, duk sai dariya ta kama Habibu, sabida wani ‘respect’ na musamman da ya lura Amirun na bashi. Ya yi fes cikin ta-zarce, na farar shadda excellencior duk da kullum cikin kwalisarshi ya ke amma Habibun bai taba ganin ya yi mishi kyau irin yau ba, to ina ga 'yammata? Wadanda ke jin kamar su ja shi ta karfi, to amma fa banda kanwar Habibu 'Mairo', wadda kallon fuskarshi ma ba zata iya yi ba idan ba dole ba. Hakurinshi ya kare, tare da duban agogon hannunshi. Shi dai kawai so yake ya ganta, ko hankalinshi ya kwanta, amma Habibu ya share shi kamar bai san halin da yake ciki ba. Cikin ikon Allah sai ga Dina ta fito daga kicin ya ce "Wai Dina ina kanwarkin nan ne?" Ta murmusa ta ce "Tana aiki ne". Tsam! Ya mike, kanshi tsaye ya doshi kicin din. Ta juya baya tana yayyanka fruits cikin wata katuwar silba, daga bakin kofa ya tsaya ya tokare hannunshi a kofar. Ya shagala sosai a cikin kallonta har ya manta abin da yake yi, bai san kuma iyakacin mintunan da ya bata a tsayen ba. Dina ta dawo ta ce "Ba ni hanya malam". Ya matsa, ta wuce ciki tana murmushi kasa-kasa, a sannan ne ma Mairon tasan da mutum a tsaye. Ta cira kai ta dube shi, shi ma duban nata yake cikin lumsassun idanunsa. Bai san me zai ce mata ba ta fahimci masifar sonta da Allah Ya dora masa. Yana daga cikin mutanen da harshensu bai iya bayyana abin da ke karkashin zuciyarsu. Sai dai action da emotion dinsu ya nuna. Da Mairon zata daure ta dube shi, da ta gane yadda ya yi laga-laga cikin SOYAYYAH. To amma ta ki, kallo daya ta yi mishi ta dauke kanta, bata sake marmarin maimaitawa ba. Ya karaso ya karbi wukar da ke hannunta ya ci gaba da yanka mata gwanda (paw-paw). Dina ta dau abinda zata dauka ta fita. Ta mika hannuwa cikin sink ta wanke hannu ta juya zata fita. Ya dago a galabaice, muryarshi har ba ta fita sosai, ya ce "Idan kika fita zan yi miki Allah Ya isa ne…, tunda Manzo ma ya ce, "BAKONKA, ANNABINKA..." Idan kika fita kin wulakanta ni, shin ma mene ne gare ni da kike guduna? Na yi miki kama da dodon da zai cinye ki ne?" Ta ja turus, ta tsaya, ita ba ta fita ba, ita ba ta juyo ba. Ya ajiye gwandar ya sha gabanta sosai har tana jin hucin numfashinsa. Wanda ke sauka da sauri-da-sauri. Kwayar idanun sun rikide, sun haukace da soyayya. Ban da alkawarin da ya daukarwa Habibu, da wallahi rungumeta zai yi, sannan ne yake jin zai iya gaya mata ko mene ne ke cin ransa, zuciyarsa da gangar jikinsa a kanta. Amma a haka ba zai iya bata bakinsa ba, ba zai iya ce mata komi ba. Da kyar ya daure ya langabar da kai, ya ce "Yi min magana mana, don Allah, Mairo? Mairo ko ba kya SO na?" Nan ma shiru, kai ka ce da gunki yake magana. Don ita jin abin ta yi banbarakwai, wai namiji da suna Hajara, tunda dai babu wanda ya taba tararta da wannan kalmar, wai….. Ya katse tunaninta da cewa, "Mairo Allah Ya jarrabce ni da sonki, tun daga lokacin da Allah Ya dora idanuna a kanki. Duk wani saukar numfashina a yanzu da sunanki yake fita, duk wani tunanina a yanzu na yadda zan mallake ki ne a matsayin matata, uwar 'ya'yana. Sunana Ameeru Abdurrahman Gaya, ni kadai ne da namiji a wurin iyayena, ina da kanne mata goma sha biyu. Na yi dukkan karatuna tare da Habibu. Iyayena ‘yan Gaya ne suna zaune a Abuja, amma mu 'yan asalin garin Gaya ne da ke cikin jihar Kano, ina aiki a Washington, sai dai kwanan nan zan bari in koma gida. Ina da mace daya da 'ya'ya zero. Duk wani abu da kike son ji game da ni, ki tambayi Habibu, zan samu karbuwa Mairo? Mairo ko ba kya so na?" Ya tsare ta da wani irin kallo daga can karkashin kasan lumsassun idanunsa. Mairo ta rasa inda zata sa kanta. Ga kunya da ta baibaye ta, ga jin nauyi, don ganinshi ta ke kamar Yaya Habibu. Idan ta ce ba ta sonshi ta yaudari zuciyarta, haka idan ta ce tana sonshi ta yi karya. Mutum daya ta ke wa 'SO' na hakika, wato UNCLE JUNAIDU. To amma shi wannan jinsa ta ke har cikin kasusuwa da bargonta ba zuciya kadai ba, da wani al'amari mai ban mamaki da ba zata iya fassarawa ba. Tunaninta shi ne, ba zata iya hada rayuwarta da kowa ba, idan ba Uncle Junaid ba. Ta dauki al'amarin da ta ke ji akan Amiru da BURGEWA da SHA'AWA, wato yana burge ta, yana bata sha'awa, yana daukar hankalinta, yana bijiro mata da sha'awar tayi aure. Zata iya aurenshi don ta mallaki gangar jikinshi, amma ba don so ba. Idan aure ne kadai hanyar da zata samu mallakar abin da zuciyarta da gangar jikinta ke so daga gare shi, to zata iya aurenshi don ta samu, amma SO guda daya na UNCLE JUNAIDU ne! Wata irin kunya ta kamata, da ta yi wannan tunanin, don gani ta ke kamar ya hango abin da ta ke sakawa da warwarewa cikin zuciyarta. Tana tunanin idan ta yi hakan kuma ai ya zama yaudara. babbar yaudara kuwa, don haka ta soma tunanin yadda zata yi ta gudu, ba tare da ta ce da shi komai ba. Yadda Uncle Junaid ya yaudare ta, ta san ciwon hakan, ko ba don komi ba don amintarsu da Yaya Habibu da mutumcin da ke tsakaninsu kamar yadda Yaya Habibu ya gaya mata, mahaifin Amiru shi ya dauki nauyin karatunsa daga masters har PhD. Sabida haka ba yadda za a yi ta yaudari Amiru wata rana ta rabu da shi idan ta samu Uncle Junaidu. Haka nan idan ta ce ta yarda tana sonsa ita ma ta yi sallama da burinta na WATA RANA zata hadu da Uncle Junaid su yi aure a lokacin da Allah Ya nufa. Gara ta ci gaba da dakon soyayyarsa, don idan ta yi aure ya tabbata ita da Junaid kenan HAR ABADA! BURGEWA da SHA'AWA ba tubala ne na kwarai da za a gina aure a kansu ba. Idan aka yi hakan, ba da jimawa ba ginin zai rushe tamkar ba a taba ginawa ba. Don haka gara ta hakura da rudin zuciya don shaidaniya ce, ta fuskanci gaskiya. Ta yi aure don Allah, ba don kyale-kyalen Amiru da rayuwa bakidaya ba. Ta ci gaba da jiran Uncle ya gaya mata da bakinsa cewa ba sonta yake ba, sannan ne zata hakura, ta yi addu'ar Allah Ya kawo mata mijin da zata so da gaskiya, ta kaunata saboda Allah, kamar yadda ta ke yi wa Junaidu. Ta daga kai a hankali ta dubi Amiru, wanda har zuwa wannan lokacin bai dauke kyawawan idanunshi daga kanta ba, binta yake da ido, da zuciya. Idan Mairo ta ce ba ta sonshi, bai san inda zai sa kanshi ba. Ta ce (cikin kaskantacciyar murya) "Don Allah ka ba ni hanya in wuce". Ya ce "Ai ba ki ba ni amsa ba, ko na yi miki tsufa ne Mairo?" "Ni ban ce ba". "To mai kika ce?" "Cewa na yi ni ba sonka nake yi ba!". Wannan ita ce kalma mafi muni da wani ya taba gaya mishi a rayuwarshi. Ji ya yi kamar ta soka mishi mashi a kahon zucci. Hajijiya ta kamashi. Ta wani fannin kuma sai ta BURGE shi, sabida kai tsaye ta gaya mishi kalmar da babu wata diya mace da ta taba gaya mishi. Wannan ya tabbatar mishi da cewa, ita ta daban ce. Sai dai yadda ta yi maganar da yanayinta kadai zai nuna maka tsabar kuruciyarta karara. Don haka bai yi fushi ba, ance wai, 'Mai nema yana tare da samu'. Ya lumshe ido ya bude su dukka a kanta "Amma mai yasa Mairo? Komi yana da dalili, kamar ni, na so ki ne sabida wasu abubuwa guda uku, wadanda bazan iya gaya miki ba. To ke mene ne naki dalilin?" Ta so ta ce da shi "Sabida ina da wanda nake so". Sai ta tuno alkawarin da ta daukarwa Yaya Habibu, na barin soyayyar Junaid da mantawa da al'amarinshi. Don haka sai ta ce. "Sabida wasu dalilan nima, da bazan iya gaya maka ba!!". Sun dauki mintina uku shiru, babu wanda ya sake cewa da dan uwansa uffan. Kamin ya dauke ido daga kanta, ya ce. "Ni kuma na yarda ki aure ni ko da ba kya sona…!!!". Ta ce "Ba zan yi hakan ba, idan na yi hakan na yaudare ka, na ci amanar kaunar da nake yi wa Uncle Junaidu……....!!!" Ta yi saurin kai hannu ta toshe bakinta da karfi, ba ta san yaushe furucin ya subuto daga zuciyarta ba, ga shi an ce 'magana zarar bunu' ta riga ta fita. Sai ya kauce da zafin nama ya ba ta hanya sabida wani masifaffen KISHI da ya taho ya tokare masa a kirji. Ai tana samun hanya ta arce. Da kyar ya iya dago matattun kafafunsa bayan mintina goma sha biyar, ya nufo falon inda ya tarar da Raymond da Habibu akan tebur suna cin abinci, Dina na tsakiyar falon tana canza channel a talabijin. Abincin da bai ci ba ke nan, ya zauna cikin doguwar kujera fuskarshi babu walwala, ya ce. "Raymond idan ka gama sai mu wuce". Habibu ya juyo ya dube shi yana nazarinsa, ya ce "Ba zaka ci abincin ba? Mairo ce ta girka maka..........." Ya dago idanuwanshi da suka canza launi luuuu! Yana kallon Habibu a kankance, ya ce "Ba zan iya ba!!". Dina ta ce "Haba don Allah Amiru? Ba ka ga wahalar da ta sha wajen girkin nan ba? Idan ba ka ci ba bazata ji dadi ba". Bai san lokacin da ya ce "Ba don ni ta girka ba, don Yayanta ne". Daga haka ya mike ba tare da ya iya hada ido da kowa ba. Ya sake ce da Raymond, "If you finish, meet me outside….". Shima Habibu sai ya ajiye cokalin don jikinshi ya yi sanyi, don bai taba ganin Amirun cikin kwatankwacin irin wannan halin ba. Don haka ya mike ya bi shi wajen ya dafa kafadunshi da ya juya baya. Ya ce. "Mai ya faru ne?" Ya kalle shi kawai bai amsa ba, tambayar duniyar nan Habibu ya yi, amma ya ce "Babu komai". Don ba burinshi ba ne a takurawa Mairo ta aure shi. So na hakika ya ke nema, ba da tallafin wani ba. Mairo da ta koma daki kwanciya ta yi, rigingine cikin nadama. Kai tsaye ka dubi kwayar idon mutum mai kima kamar Amiru da ya ce yana sonka, ka ce ba ka son shi, ya zama wulakanci da cin fuska. To amma ita a ganinta dai-dai ta yi, don ba ta iya karya da yaudara ba. Amma dai duk da haka ta san ba ta kyauta ba, sai dai a ganinta gara hakan, da ta yi irin auren da zuciyarta ta raya mata. Dina ta yi sallama ta shigo, dauke da faranti tana cewa "Kin yi barci ne?" Ta girgiza mata kai, alamar "A'ah". Ta ce "To tashi, abincin da kike gudu ne na biyoki da shi". Ta tashi ta zauna sosai, ta karbi farantin ta soma ci, Dinan na kallonta. Can kuma ta ce "Mairo mai kika ce da Amiru ne? Ya shigo cikin walwalarsa, ya fita cikin yanayin da bamu taba ganinsa a ciki ba. Ina laifin wanda ke son ka?" Ta cira kai ta dube ta, sai kuma ta sunkuyar. Can kuma ta dago ta dube ta, ta ce "Yana magana ne akan wai yana sona, ni kuma na gaya mishi cewa, bana son shi!" Dina ta yi murmushi. Daga jin kalaman Mairo, da yanayin maganarta kasan kuruciya ke dawainiya da ita. Ta ce "Sabida mai ba kya sonshi Mairo? Ga shi kyakkyawa, son kowa, kin wanda ya rasa. Ga shi da ilimi kamar Yaya Habibun da kike cewa yana burge ki. Yana da mata Baturiya, amma ya tsallakota ya zo ya ce yana sonki. Zai iya rabuwa da ita sabida ya aure ki. Ga shi da kirki, ga addini. Ke kuwa mai kike nema a da namiji da ya wuce wannan?" Sai Mairo ta sa kuka. Ta kwantar da kai a cinyoyin Dina, tana kuka mai tsuma zuciya. "Na kasa mance Uncle Junaidu ne Aunty Dina. Na kasa mance dumbin alherin da ya yi min a rayuwa. Shi ne tsanin duk wani matsayi da matakin da nake kai a yau. Idan na auri wani ba shi ba, na ci amanarsa…...." Dina ta katse ta "Akwai hanyoyi da yawa da zaka saka wa mutum alherin da ya yi maka ba dole sai ta hanyar aure ba. Misali shi ne, ka dinga binshi da kyakkyawar addu'a ba tare da shi din ya sani ba. Wannan addu'ar Allah Ya yi alkawarin karbarta. Kada ki yi mamakin zuwa yanzu shi Junaidun ya samu wata da yake so ya aura. Ni na kasa gane kan wannan soyayyar da kike yi wa Junaid, maras dalili. Kin ce bai taba cewa yana sonki ba. Kin ce ba ku yi alkawarin aure ba, kin ce yasan gidan Baffa, amma bai neme ki ba. To ki gaya min wacce hujja gare ki da zata tabbatar da cewa yana sonki? Ba ki san akwai masu taimako sabida Allah ba, ba don a aure su ko a saka musu da soyayya ba? Haba Mairo, ki yi tunani mana? Ki yi aiki da hankalinki. Ki so mai sonki a zahiri da badini. Ki yi aure saboda Allah da raya sunnar ma'aiki, amma ba don abin da zuciyarki ta afu akai ba. Mai yiwuwa ne shi wannan abun da kika kwallafawa ran ba alheri ba ne a gare ki, wanda ba kya so din shi ne alherin. Idan kika fauwalawa Allah a hankali za ki so abun, tunda shi ma Junaid ba lokaci daya kika fara sonshi ba, so na soyayya, kin ce sai da tafiya ta yi tafiya kika mallaki hankalin kanki, sabida fahimtar halayenshi da kika yi. Shi ma Amiru a hankali za ki fahimce shi, kuma ki so shi wallahi fiye da son da kike wa Junaid ma. Ba ki ci amanar Junaid ba, ba ki yaudare shi ba tunda ba alkawari kuka yi ba. Iyakar soyayya ta gaskiya kin yi wa Junaidu, ko ba ki aure shi ba Allah Ya shaida ya yi alkawarin sanya masoyan gaskiyan da suka mutu ba tare da sun auri juna ba a aljanna. Ina tunanin Junaid ya yi abin nan ne da Hausawa ke cewa, "A BARI YA HUCE... SHI KE KAWO DA RABON WANI". Ta dubi Dina sosai, ta ce "Idan haka ne Aunty Dina, kema kin yarda Uncle Junaid yana sona? Furtawa ce bai yi ba, kamar yadda Inna da Nabilah ke cewa?" Gyada kai Dina ta yi, ta ce "Eh, yana sonki, amma ya bari YA HUCE... Don babu wata mu'amala ta mutumci da tausayi tsakanin mace da namiji sai SOYAYYAH! Idan ma mutumcin ne da farko, to daga baya rikidewa ya ke ya koma soyayya. Kuma dama ita irin wannan dadaddiyar soyayyar ba a fiya auren juna ba. Wasu ma har su mutu, ba sa kara ganin juna. Wasu kuma daya ne yake mutuwa ya bar dayan cikin soyayyar, kuma babu yadda dayan zai yi, a karshe dole zai hakura ya auri wani, wasu kuma hakura suke da auren har zuwa sanda nasu ajalin zai riske su. Amma Ubangiji ba ya son hakan, don haka bana son ki zamo daga cikin wadanda za su kyamaci sunnar Ma'aiki sabida soyayya. Manzon Allah (S.A.W) cewa ya yi "Ku yi aure don ku hayayyafa... Bai ce ku yi aure don soyayya ba. Karewama, duka matan ma'aiki da dalilin da ya yi sanadin da ya aure su, ba soyayya ba. Soyayyarsu tana kafuwa ne a hankali cikin gidan aurensu. Ki yi koyi da Nana Khadijah wadda halayen amana na Ma'aiki ya kwadaitar da ita ga son aurensa, shi ma kuma ya aure ta don dukiyarta, addininta da nasabarta. Ki auri Amiru don yana da nasaba, addini, ilmi da arzikin ma, ku raya sunnah ku haifi 'ya'ya ku yi musu tarbiyyar musulunci in gaya miki karshen soyayya ke nan. Ke nan har wata soyayya kika sani ko halarci? Wallahi HALACCI kike yi mawa ba SOYAYYA ba. Amirun shi kike so da gaske, na gani a kwayar idonki, na gani a gangar jikinki. Kina jin abubuwan da kike ji kan Amiru a Uncle Junaidun? Kina neman Junaid ya aure ki ne don ya tallafi rayuwarki a lokacin da kike neman matallafi, amma ba don kin san hakikanin me aure ya kunsa ba. Kina so ki ramawa Junaid halaccin da ya yi miki ne ta hanyar 'aure' don da shi kika saba, ya sanki, kin sanshi, a tunaninki wannan shi ne karshen soyayya, to ba shi ba ne, soyayyar aure daban ta ke, Allah ke hadata, kuma bata fassaruwa. Haka ita ma kauna daban ta ke, sai kin auri Junaidun za ki ji kamar kin auri Babanki. A sa ma shi din ya ce yana son naki, balle bai ce ba. Tsayin shekara biyun nan wallahi da duk inda kike ya neme ki, da fa ya damu da ke. Ita zuciya an halicce ta ne da son mai kyautata mata, wannan shi ne tsakaninki da Junaid ba soyayyar aure ba. Idan kuma mata sun fara zuwa neman aure ne, to sai mu je gidansu mu neme shi mu kai kudin aure, mu gaya mishi yadda kike sonshi har kina gayawa masu sonki da auren, ke ba kya sonsu, sabida kar ki ci amanar soyayyar sa da ya ba ki…..." 8/2/21, 10:31 PM - Kawata: G Ala dole ta murmusa, don tasan zambo ne take mata. Duka wannan bata lokacin da Dina ta yi tana bayani, ba duka abin da ta ce ne ta yarda da su ba. Ta dauki Dina a matsayin mai campaign ga Amiru, sabida shi ta sani, shi ne mai irin tsarinm rayuwarsu. Ita kudin Yaya Habibu ma tsoro ya ke bata, balle na Amirun da ta sha jin suna cewa yana world bank, karewar Barclays. Ta yarda ta hakura da Junaid sabida kwararan hujjoji masu karfi da kowa yake gaya mata, hatta Nabilah. Ta ce da ita lokaci ya yi da ya kamata ta manta da soyayyar da ta ke wa Uncle Junaid ta yi aure. Ta dubi irin auren da ita ta yi, amma ga shi ya zame mata ALHERI, don yanzu ba abin da ta ke so a duniya sama da mijinta, kuma shi ma hakan har ga albarkar haihuwa. Ta sauke ajiyar zuciya, ta koma ta kwanta a gadonta, ta ja bargo har kanta. Barci ta ke so ya zo ya dauke ta, amma ya ki zuwa. Al'amarin na neman tarwatsa mata kwakwalwa, tareda wargaza mata tunani. Tana son ta yarda da Dina, halaccin da ke zuciyarta na karyatawa. Amma abubuwan da ta zana ai duk haka suke, zata je neman auren Uncle Junaid ne? Ko haka zata kare da zaman jiran tsammanin warabbuka? Zata iya ci gaba da zaman jiran ranar da Junaid zai neme ta, ya bayyana mata soyayyarshi, ya ba ta uzurin da ya hana shi yin hakan har nan gaba da abada. Amma ba zata iya jure bukatar gangar jikinta da zuciyarta ba, kamar kowanne lafiyayyen dan Adam. Idan haka ne tana bukatar aure, domin kare kanta daga ZINA, da sauran ayyukan ALFASHA, cikar mutunci a idon duniya, da karuwar matsayi a fadar Ubangiji. Wayarta da ke karkashin filo ta soma dan kidi mai sanyi, alamar shigowar sako (text). Cike da mamakin wanda ya yo mata sako a dai-dai wannan lokacin, karfe biyu na sulusin dare agogonsu na can. Ta mika hannu ta lalubo wayar ta danna, ba tasan lambar ba, don bakuwa ce. Ga abin da ke rubuce. '... When life change, and we go our separate ways, U will still be in my heart till my dying days... My world has never meet a person like U……...! (A yayin da rayuwa ta canza , ni da ke muka bi hanyoyin mu mabambanta (muka rabu), za ki cigaba da zama a xuciyata har karewar numfashi na. Duniyata bata taba haduwa da mutum irin ki ba). Haka ta sa sakon a gaba, tana ta karantawa. Har aka yi kiran assalatu. Don ta tabbatar ba kowa ba ne, Amiru ne, duk da bai sa suna ba. Allah sarki ko YA HUCE ne? Ta fada a fili. Tana so ta ba shi amsa, ba ta san me zata ce masa ba. Da safe ta ke nunawa Dina, ta karanta, ta yi dan miskilin murmushinnan nata, ta ce. "Ke kuma kika ce mene?" Ta zumburi baki. "Ni ko kulasa ma na yi?" Ta yi dariya, ta na kwaikwayon ‘yar muryar ta tace, "Haba Mairo? Yi hakuri ki dan kula sa. Kinga shi ya yi fushin amma ya sauko, saboda ya gane ba son sa ne ba kya yi ba, kawai ke mai aminta amana da alkawari ce!". Ta yi dariya har kumatun ya lotsa, Dina kam akwai shegen wayo, kanwa ce uwar gami.. Ta ce "To me zan rubuta?" "Ki ce kawai ya zo yayi joining dinmu break fast…..". Ta rubuta ta tura, amsar da ya ba ta ta sata yin murmushi. Domin ya ambato rabin-ranta (uncle Junaidu). "...A'ah kirawo Junaid….". "He is far-away...!!"(Amsar Mairo ) "And am not closer too... am far-away either, and I'll not come back...!!! On my way to Detroit Metro…...". Hankalin Mairo yayi mummunan tashi, da sauri ta jefar da wayar, da gudu ta yi daki ta dauko mukullinta, Dina na kira amma ba ta juyo ba, cikin rishin kuka ta ce. "Shi ma zai tafi ya barni, kamar yadda Junaid ya gudu ya barni. Bayan sun kimsa min soyayyarsu. Bana son in samu wannan heart break (karyewar zuciyar) a karo na biyu". Dina ta ce "Bishi Mairo, shi ne ZABIN ALLAH!!" Gudu ta ke shararawa akan titin da zai kai ta airport din Detroit. Cikin kankanuwar motarta GMC Terrain. Hawaye na sauka akan kundukukinta. Da gaske Dina ta ke, Wannan ita ce soyayyah! Da gaske Dina ta ke, Amiru shine zabin Allah!! Da gaske Dina ta ke da ta ce ta kama mai sonta, ta rabu da JIRAN TSAMMANIN WARABBUKA. Ta karbi 'Soyayyah' a hankali zata rikide ta zama 'Kauna'. To gashi soyayyar ma zata tafi ta barta da tsammanin warabbukanta wanda bata fata…….… Koda ta iso airport din ko kulle motar ba ta yi ba, a jikin motar ta bar mukullin. Da gudu ta sheka cikin reception tana dube-dube, babu Amiru, babu ko mai kama da AMIRU. Ta karasa terminal bayan ta hankade ma'aikacin da ke kokarin hanata shiga. Dai-dai sanda aka rufe kofar jirgin (Lufthansa), wanda zai tashi zuwa kasarmu mai dumbin albarka. Ba da jimawa ba kuma ya soma ruguginsa mai gigitarwa bisa kwaltarshi. Kafin ya dai-daita sosai, a sararin samaniya. Mairo ta durkushe a nan tana kuka, kukan da ta dade batayi irinsa ba tun bayan rashin BABANTA da INNAR TA. Fita yake tun daga karkashin zuciyarta. Amiru ya tafi tareda dukkan farin cikin da ta samu cikin Michigan wanda Habibu ya dade kafin ya assasa. Bai shigo rayuwarta da sauki ba ashe! Ashe ya shigo ne don ya rusa komai . Ya tafiyar da sauran karfin zuciyarta. Ya dawo da rayuwa unbearable kamar Uncle Junaidun? Meyasa ita ba ta da sa’a ko kankani a soyayya ???. Ji ta yi kamar an tsugunna a gabanta, kamin ta dago kuma, an kai hannu a hankali an dafa kafadarta. Don haka ta dago idanunta jage-jage da hawaye... don ganin ko wane ne wannan??? Masha Allahu La Kuwwata Illa Billah! Mu biyo Mairo da Amiru da Junaidunta a littafi na uku. Kafin nan ina sauraron ra'ayoyinku kan jaruman namu, AMIRUN ko JUNAIDUN??? Maman SAFAH da MARWA ce. 07030137870 8/3/21, 12:25 PM - Kawata: 444 Ta dago idanunta jage-jage da hawaye, don ganin ko wane ne wannan? Da haka kawai zai zo ya dafata? Ko ta ce da wani tana neman taimako ne? Wa za ta gani? Yaya Habibu ne! Cikin matsanancin mamaki ya ce, "Mairo?" Ba ta amsa ba, illa ta bi shi da kallo, da jajayen, idanunta. Ya sake cewa "Me ya kawo ki nan? Ina za ki je?" Nan ma shiru ta yi masa, sai kallonsa ta ke kamar ta rufe shi da duka don haushi. Ya ishe ta da tambaya, ya barta ta ji da kukan zuci, da takaicin da ya dame ta. Don ji take kamar Amiru ya bula mata kura, ya ja motar rayuwarshi, ya barta. A nashi bangaren, shima Habibun, haushi ne ya kama shi, ya ce "Kina ji ina magana kin yi kunnen uwar shegu da ni? Na ce me ya kawo ki nan, kuma gurin wa kika zo? Ina zaki je?" Nan ma shiru ta yi masa, kamar da dutse yake magana, kuma ba ta dauke idanunta daga kanshi ba. Ta kafe shi dasu kurrrrr! Kamar shi ne ya kori Amirun. Iyakar fusata Habibu ya fusata, ya fizgi hannunta suka fito harabar adana motoci na airport din, yana baza ido don gano inda ta yi fakin. Daga can ya hango motar ta yi mata wani banzan fakin a inda aka rubuta no parking, Security ne cikin fararen kayan ma'ikatan gurin tsaye jikin motar, wato sun kamata. Ya yi tsaki, tsut…, suka doshi wajen, har yanzu yana rike da hannunta, sai janta yake kamar kayan wanki. Ya mika hannu ya zare makullin ya soma ba su hakuri ya nuna musu Mairo ya ce ga dukkan alamu ba cikin nutsuwarta ta ke ba, su yi mishi uzuri su ba shi motar. Abinka da malam bature da bai san cin hanci da rashawa ba, gami da bin ka'ida da dokar duk da aka shimfida masa, kememe sun ki yarda, sun dage dole su dangana da ofishinsu in har suna son motar su, don a ka'ida mai matsala a kwakwalwa, ba a yarda ya tuka abin hawa ba, ya ce lafiyarta kalau, tension ne kawai, suka ce idan haka ne ke nan tana sane ta karya musu doka? Don haka dole su dangana da ofishinsu, amma ba zasu bada motar ba. Cikin matsanancin fushi, Habibu ya dubi Mairo "Kin kyauta, kin ga abin da kika jawo min ko? Yau shekaruna goma cur cikin kasar America, ban taba zuwa ofishin 'yan sanda ba, don haka sai ki bi su ku je, ki yi musu bayanin dalilinki na karya dokarsu, tunda ni kin yi min banza, sai ki je ku karata.......” Ya cika hannunta zai tafi, ta riko bayan rigarsa tana kuka. Ya ce "Wallahi bazan je ofishin 'yan sanda ba, sai dai ki hakura da motar, ki bar musu mu tafi, kuma wallahi-wallahi ba zan sake siyan wata ba". Ta ce ta yarda, don haka suka bar motar a nan, suka nufi motar Habibun. Allah Sarki, dan uwa rabin jiki! Sun yi nisa sosai danja ta tsaida su, ya saci kallon Mairo da ke kujerar gefensa, ya ga har yanzu kuka ta ke mara sauti, ta rufe fuska da mayafinta. Sai ya hadiye fushinsa, ya soma lallashinta cikin dabara. "Ni dai idan don na tambaye ki inda za ki ne kike min wannan kukan, to ki yi hakuri. Mantawa na yi, ashe fa Amiru ya fada min ba kya son tambaya. Ban da abinki Mairo, idan wajen Junaid kike son zuwa, jirgi ya tashi ya barki, ai sai ki fada mini, na yi miki booking din wani, amma ba ki sunkuya cikin dubban mutane kina rafka kuka ba, kamar wata mai tabin hankali. Yana ina Junaid din? Nigeria ko Russia?" Cikin kuka ta ce "Ni fa tunda na yi maka wancan alkawarin, ban sake tuna zancen Uncle Junaid ba". Ya ce "To ina za ki? Ko AMIRU kika biyo?" Hantar cikinta ta karta, ta rasa me zata ce masa, don haka ta ja bakinta ta yi shiru. Habibu ya kuta ya ce "Hakan da kike yi, kina ganin mutumci za ki sayawa kanki? Shi wancan bai ce yana sonki ba, sabida neman gindin zama kika kwashi jiki kika je gidansu don rashin hankali da rashin mafadi. Shi wannan da ya ce yana sonki, kin ce ba kya sonshi, sabida kar ki ci amanar wanda bai ce yana sonki ba. Ya hakura ya bar miki kasar ma baki daya ba garin ba. To uban me kika biyo shi ki mishi? Da kin same shin me za ki ce masa? Yi hakuri na tuba, ka zo ka aure ni ko me? To ni bana son rashin hankali da rashin mutunta kai, aikin zubar da kima, da wulakanta kai. Kin riga kin ce ba kya sonshi, to a barshi a hakan. Allah Ya kawo miki wanda kike so. Don wanda ya ce ba ya sonka tun farko, daga baya ya dawo ya ce yana sonka, to akwai dalilinshi na yin hakan. Wato za ki yi A RASHIN UWA... akan yi UWAR DAKI...? To ba da abokina ba! Idan auren kike so ki yi, ki je ki nemo Junaidun, tunda ba kya son karatun da nake sonki da shi. Abu na dan lokaci kalilan, ba zaki maida hankali akai ba, mazan nan da kike gani, dukkansu matsala ne, shi kansa auren idan ba a tsaya anyi shi cikin nutsuwa ba, babu inda ya ke zuwa. Don haka yarinya, kama kanki. Wayar ma daga yau ba zaki sake rikewa ba, kamar yadda babu ke babu tukin mota. To kin ji". Dai-dai lokacin da ya yi fakin a harabar gidansu, ya juya bayan motar ya dauko falmaran din suit' dinshi da wayoyinshi ya fito, ita ma ta fita, ba tare da ta yarda sun kara hada ido ba. Dina ta tari mijinta kamar yadda ta saba a kullum, amma ya sakar mata harara. Ya fincike jikinsa daga jikinta ya juya ya kara hararar Mairon da ke shigowa sumui-sumui kai a kasa, kamar wata munafuka, ya dawo da dubansa ga Dina. "Da saninki Mairo ta dauki mota ta tafi airport?" Dina ta yi shiru, ya ce "Magana nake, ko ke ma sullutun za ki mayar da ni ku barni na yi ta magana ni kadai?" Ta ce "To me ya faru?" "Ya zan tambaye ki kema ki tambaye ni? Amsa nake son ji kawai, kina sane ta tafi ko a'ah? Yanzu na je kai Amiru zai tashi zuwa Najeriya na ganta tana kuka akan titi uban me ta je yi?" Dina ta hau kame-kame ganin yadda ya hasala sosai, ta ce "Am... Eh, ai sako zata kai wa Amirun". A fusace ya ce "Sakon me?" Ta ce "Ka ga Allah ban sani ba, can tsakaninsu". Ya yi dogon tsaki, ji kake 'tsiiittt!' Ya maida kallonshi ga Mairo "Ba ni wayarki". Ta soma dube-dube a falon inda ta cillar da ita, can ta ganota bayan room heater, ta dauko ta mika mishi. Ya kashe ta gaba daya ya jefa a aljihun wandonsa da sassarfa ya nufi bangarenshi ya barsu nan tsaye cirko-cirko kamar an dasa su a wurin. Dina ba ta yi gigin binsa ba, don tasan halin kayanta sarai, idan ya yi fushi yana bukatar a daga mishi kafa, har sai ya sauko don kansa, wanda ba ya daukar dogon lokaci yake yin hakan. Ba ya son aje ana wani lallashin shi ko ace za a ba shi hakuri. Ta kama hannun Mairo suka nufi dakin Mairon suka zauna a bakin gado. Ta ce "Kin same shi?" Ta girgiza kai, wasu hawayen suka zubo. Dina ta sa yatsunta tana share mata, "Kada ki yi kuka Mairo, mika dukkan lamurranki ga Allah. Amiru yana sonki, na kuma tabbata zai dawo. Shi ma Junaid yana sonki, ina tabbatar miki da shi ma akwai ranar da zai zo. Allah kadai Ya san mijin ki a cikinsu, don haka ki dukufa ga neman ZABIN ALLAH ba zabin zuciyarki ba". Don haka Mairo ta tattara shawarwarin iyayen rikonta, wato masoyan nan nata guda biyu, da ba ta da ya su a duniya: Yaya Habibu, da Maidakinsa, Dina. Ta karbi shawarwarin su da hannu bibbiyu, ta fuskanci jarrabawar karshen shekara da ta tunkarota, wadda daga ita zata shiga shekara ta uku, kuma ta karshe da zata hada digiri dinta. *** A yau suna da tutorial class, kan wani kwas da zasu fara jarrabawa a kanshi. Mairo ta fi duk 'yan ajin su fahimtar wannan darasin, don haka suka bukaceta da ta yi musu karin bayani. Maryam Muhammad Bedi, ta fito gaban ajinsu ta tsaya rike da takardu, domin wani abu ne da ta kware a kai, wanda Uncle Junaid ya koyar da ita, wato dabarun speech in public, ba tare da jin ko da dar a zuciyarta ba. Ta soma feso sassanyan Turanci daga makogaro zuwa harshe, sannan siraran labbanta su furta. Kai ka ce diya ce ga Herbert Spencer. Tana bayani ne akan Segmund Freud's stages of psycho-sexual development, tana farke theory tana yin kaca-kaca da ita tun daga phallic-stage... Anal stage... da 'yan uwansu. Sannan ta koma kan SOCIAL CLASSES; the BOURGEOISIE and the PROLETARIAT………. !!! Habibu da ke cikin 'yan ajin ya sanya mask (fuska) sai ya soma kuka. Sannan ya taso ya fito, zuciyarshi cike da alhinin ina ma ace... Malam Muhammad Bedi, zai dawo duniya yau ya ga Mairon shi na koyar da turawa, da sauran jinsin al'umma. Don haka Mairo yau da ta dawo gida ta ga sauyi sosai daga Yayan nata. Domin dai ya tabbatar ta tsaida hankalinta tana karatun, kamar yadda yake so. Yaje makarantar ne ya shiga cikin ‘yan ajinsu don yayi supervising hakan. Shi da Dina ne cikin three seater suna aiki cikin takardu da kwamfuta. Ya daga kai ya dube ta yana murmushi, a lokacin da tayi sallama ta shigo. "Mairo 'yan makaranta......Mairon Dina….. Mairon Yaya Habibu". Ta yi murmushi, har kumatun ya lotsa. Za ta wuce cikin daki ya ce. "Zo zauna, mota zan sake miki". Da hanzari ta dago ta dube shi. Ya daga mata gira (in affirmation) watau cikin tabbatarwa "Gaya min duk irin motar da kike so ni kuma na yi alkawarin zan yi kaffara in saya miki. Sannan ki mai da walwalarki kamar da, bana son ganin wannan shiru-shirun da kika koma. Sannan Dina ta fada min ko hira kin daina yi da ita, kullum sai karatu. A dinga rage karatun, a dinga baiwa zuciya da kwakwalwa dama su huta, sai karatun ya fi zaunawa sosai. Zan tafi Nigeria gobe, akwai muhimman al'amura da zamu gabatar ni da Amiru a Abuja, zan yi sati daya, me kike so in kawo miki? Dina ta rubuta min kayan abincinmu na gargajiya su kuka, daddawa, rogo, kubewa da sauransu. Ke kuma fa?" Ta yi murmushi kanta a kasa ta ce, "Ladidi nake son gani". Ya ce "Ai an yi mata aure. Kina ganin zan rabo mace da gidan aurenta ne na kawo ta? Ai mijinta ba zai so ba, ki yi hakuri ki kare karatun gida za mu koma gaba daya. Gobe sai ku je da Dina ki zabo motar da kike so, zan bar komai a hannunta". Ta yi godiya, ta kama hannun Little Mairo suka nufi dakinta. Dina da Habibu suka bita da kallo, dukkansu ba haka suke son ganinta ba. Gaba daya ta sauya, tun ranar da Amiru ya tafi, daga daki sai daki, daga littafi sai littafi na gaggan malaman sociology. Habibu na addu'ar Allah Ya sa ba sociology'n ne ya soma taba mata kwakwalwa ba. Shi yasa tun farko bai so ta zabi wannan kwas din ba, amma ta dage ita nan duniya shi ta ke so, ba don komai ba sai don ta zama Uncle Junaidu. Ita Dina da yake tasan dawan garin, wato Mairo ta soma kamuwa da matsananciyar soyayyar Amiru sai ba ta damu sosai ba. Habibu ya daga Nigeria a washegari, da tsarabar Baffa da iyalinshi rankatakaf! Da aiken Mairo ga Ladidi. Ita da Dina suka shiga gari suka yo cefanen kayan abinci da kayan amfanin gida da ya kare, sannan suka nufi wani kamfanin motocin (General Motors) dake nan cikin Michigan ta zabi mota irin tata ta da, watau GMC Terrain ruwan makuba, suka shirya payment Dina ta biya, ta karbo rasidi da takardun mota aka biyo su da ita gida. Duk a kokarinsa na son farantawa 'yar uwarshi, yana sauka a gidan Baffa ya kira wayar Dina, ko gaisawa ba su yi ba, ya ce ta hada shi da Mairo, ga Ladidi ga Baffa. Farin cikin da Mairo ta samu kanta da jin muryar Baffa da Ladidi ba zai fadu ba. Sun dade suna hira, inda Ladidi ke sanar da ita tsohon ciki ne da ita, ta yi mata fatan sauka lafiya, sannan ta baiwa Dina suka ci gaba da hira ita da Habibu. Washegari Dina ta kira shi don su gaisa, amma wayarshi a kashe, sai ba ta damu ba, ta ci gaba da ayyukan gabanta. Karfe biyu na rana agogonsu na can, ta sake gwadawa ko za ta samu, amma wannan karon ma an sanar da ita wayar a kashe ta ke. Yinin ranar zungur, haka ta yi ta nemansa amma ba ta samu Habib ba. Abu kamar wasa, har kwana uku ba su samu wayar Habibu ba, sannan ita ma idan ta buga ba ta shiga. Hankalinta ya tashi, amma ba ta bari Mairo ta gane ba. A rana ta hudu ne dabara ta zo mata. Ta kira layin Baffa, bayan sun gaisa ta ce, ko yana da labarin Habibu? Sun kasa samunshi a waya. Baffa ya yi gyaran murya ya ce "Tun ranar da ya zo, ya samu sakon cewa amininshi Amiru ba lafiya, don haka ya tafi Abuja wajenshi ban san halin da suke ciki ba". Dina ta yi zugum! Da waya a hannu, tunani iri-iri babu wanda ba ta yi ba. Ba ta fatan ya kasance ciwon Amirun yana da alaka da soyayyar Mairo. Ta sanshi bai iya daukan al'amuran rayuwarshi da wasa ba. Idan ya ce, yes to da gaske yana nufin yes din, babu gudu babu ja da baya, raba shi da abin nan da yake so sai wani babban ikon Allah. Sannan Amiru mai-nasara ne, bai taba sanya abu a gabanshi ya kasa samu ba. Jin motsin fitowar Mairo daga kicin ta yi azamar sauke taguminta ta kakaro murmushi, wanda iyakacinsa fatar bakinta, ta ce "Baffa yana gaishe ki, yanzun nan muka yi waya da shi". Ta aje farantin da ke hannunta akan centre-table, ta ce "Ina amsawa. Ni Yaya Habibu lafiya dai ko? Tun ranar da ya tafi har yau ban kara jin wayar shi ba". Dina ta shirga karya "Am, eh, ya kira kina barci ne shi yasa ban tashe ki ba". Ta ja farfesun kifin da Mairo ta aje mata, ta soma shan romon da cokali. Tana satar kallon Mairo ta wutsiyar idonta. Wadda ta maida hankali ga labaran CNN da Mu'azzam Kanti, ke kwararowa. (Alkawari bayan rai). Amma a zahiri ba sauraronsa ta ke ba, kewar dan uwanta ne ya dame ta, da rashin jin dadin rayuwar ko ta yaya, da ta samu kanta a ciki. Ba ta rasa ci ba, ba ta rasa sha ba, mai kyau kuma mai dadi, amma zuciyarta a kuntace ta ke babu dadi. Tana ji a jikinta wani bakon al'amari mai GIRMA na shirin faruwa da ita, wanda ba zata ce mene ne ko na mene ne ba. Washegari da asuba bayan ta idar da sallah, ta yi azkar din safiya kamar yadda ta saba. Ta yaye labulen dakinta tana kallon yadda snow ta yi musu lullubi. Amma hakan bai hana Bature yin harkokin gabansa ba. Yau ranar ta kasance lahadi, don haka ba zata je makaranta ba, kai kofofi da tagogin gidan ma duk lullube suke da dusar kankara. Room heater da ke aiki a dakin bata taimaka ba ko kankani wajen rage azabtaccen sanyin da ta ke ji ba, wanda idan da sabo, to sun saba. Ta hau kwamfuta don duba emails dinta. Bayan ta yi wa sanyi mugun shiri cikin bakaken coat da bakin wandon jeans mai kauri, hand-socks (safar hannu) da leg-sock (safar kafa) duk bakake wul. Sakonnin suka soma bayyana, inda welcome-screen ke tabbatar mata tana da sabbin sakonni guda goma sha biyar. Ta soma budawa, yawanci duk daga Nabilah suke, tana tambayarta abin da ya samu wayarta ta kasa samunta. Ta mayar mata da amsa cewa, ta yiwa Yaya Habibu laifi ya kwace, sai na Ir’eesh inda ita kuma ta ke sanar da ita cewa akwai test' karfe sha biyu na ranar washegari, wato litinin. Sai na wani dan ajinsu Henry baturen Brussels inda yake sanar da ita ya wuce kasarsu don mamarshi ta rasu. Ta taimaka tayi masa wani assignment, ya neme ta a wayarta bai same ta ba. Ta yi mishi ta'aziyya ta tura, sai wani guda daya da ya yi matukar daukar hankalinta, kasancewar an yi shi ne cikin harshen Hausa, da rubutu in italic, sannan babu sunan wanda ya aiko, sai logo na hular ilmi. Ta soma bin rubutun a gurguje. "Nasarar dan Adam a rayuwa, ana gane ta ne tun daga kuruciyarshi. Mutanen da suka samu kansu cikin gwagwarmayar rayuwa daga yarintarsu zuwa giramansu ba sa karewa haka a banza. Ina da yakinin cewa, kina daya daga cikinsu, ci gaba da kokari har sai kin cimma burinki na zama ‘malamar makaranta’, kada ki bari soyayyar da ke zuciyarki ta zamo barazana ga ci gaban rayuwarki. Dora soyayyarki akan turba ta hankali da tunani, ba don fita daga wani kunci ko matsatsi na rayuwa ba". -mai son ki. Ta karanta ya fi cikin 'ya'yan carbi, amma ba ta fahimci me mai sakon ke son isarwa gare ta ba. Wa ya ce da shi tana cikin soyayya ko cikin matsin rayuwa? Ta yi tsaki mai karfi ta goge sakon daga cikin akwatun adana sakonta, amma ba ta iya ta goge shi daga kwakwalwarta da zuciyarta ba. To haka washegari, mai 'logo' na hular ilmi ya sake turo mata da gajeren sako. "........ Some one misses you!". Abin sai ya koma ba ta haushi, wannan karon ma ta goge ba tare da ta ba da amsa ba. A ganinta ko waye, yana son yi mata yawo da hankali ne. Ta so ta fadawa Dina, amma ganin Dinar kwana biyun nan ba ta cikin walwala sai ta kyale ta. Karfe tara na daren ranar, suna bisa tebir dukkaninsu, har yaran, suna cin abincin dare, daga can kicin Lynder ke ta goge-gogenta. Wayar Habibu ta shigo wayar Dina, kar ku so ku ga mazari a wurin Dina garin rawar jiki ta datse kiran da hannunta. Ya sake kira a karo na biyu, wannan karon Allah Ya ba ta ikon amsawa. Muryarshi ba ta fita sosai, kamar mai fama da mura ya ce "Yaya kuke? Ya Mairo da yaran?" Ta yi ajiyar zuciya ta ce "Duk lafiya muke. Haba Habib? Ka barmu cikin fargaba. Akalla ko mene ne ya faru da kai ka daure ka sanar da ni, sannan ka kulle wayar. Duk kwanakin nan hankalina a tashe ya ke". Ya ce "Ki yi hakuri, bana cikin hayyacina ne, I don't want to lose AMEERU. (bana so in rasa Ameeru). Ki debo passport dinku a dakina, daga gobe zuwa jibi ku nemi jirgi ku taho, ki kai yaran gidan Sultana sabida makaranta, ku taho ke da Mairo". Dina ta kidime "Lafiya? Me ya faru da Amirun?" Bai ba ta amsar ko daya ba, ga dukkan alamu kuka Habibun ke yi kasa-kasa, wanda ba ya so ta jiyo. Hankalinta idan ya yi dubu ya tashi. Ba kankanin abu ke sa Habibu kuka ba. Kada Allah Ya sa abin da ya darsu a zuciyarta yanzun ya zam tabbatacce. 8/3/21, 9:03 PM - Kawata: B Cikin dauriya ta ce "Habib, me ya faru da shi? Ka gayamin don Allah. Sai dai na taho ni kadai, Mairo jarrabawa zata fara zanawa, wadda idan ba ta yi ba, sai ta maimaita shekarar". Da budaddiyar murya ya ce. "Karatun ma, ai ina jin ta barshi kenan. AURE zan yi mata". Dina ta kyafkyafta 'yan idanunta ta sato kallon Mairo, cike da fargabar Allah Ya sa ba ta jiyo abin da Yayanta ya ce ba. Ta ga hankalinta ba ya kanta, ya tafi ga lallashin Little Mairo ta ci abincin da ta ke ba ta da dan kankanin cokali. Ta godewa Allah da abin da ya darsu a ranta (mutuwar Amiru) ba shi ne ba. Ta kawo gwauron numfashi ta ce "Kano za mu taho ko Abuja?" Ya ce "Ku biyo jirgin Abuja, idan kun sauka ki kirani zan zo na dauke ku". Don haka a daren yau bakidayansa Dina ba ta samu isasshen barci ba. Tausayin Mairo ya cika mata zuciya. Irin yadda ta ke wahala akan karatun nan, ta kwallafa rai a kansa, kullum cikin ‘solving assignments' ace ya tashi a banza! Shekaru biyu cur! Sai dai kwarin gwiwar da ta ke da shi, shi ne Habibu ba zai kai 'yar uwarsa inda za ta tozarta ko ta wulakanta ba. Duk son da ta ke yi mata ta tabbata bai yi rabin-rabin wanda shi yake yi mata ba. Sannan akan Amiru ba abinda bazai iya ba. Da safe karfe takwas ta yi shirin fita don yi musu booking din tickets na jirgin ‘Lufthansa’ wanda zai tashi karfe goma na daren ranar. Sannan ta dawo, ta cimma Mairo ta fito daga wanka tana shafa akan stool ta ce (tana mai kawas da kai) "ki hada kayanki masu dan yawa, gida Najeriya zamu tafi, ban san kuma ranar da zamu dawo ba". Tana mai kawas da idanunta daga gare ta, don ba zata iya fada mata abin da Habibun ya gaya mata ba. Cikin mamaki Mairo ta ce "Me ya faru? Irin wannan tafiya haka unexpected?" Dina ta ce "Bai fada min ba, amma dai ya ce lallai mu tafi". Kamar ta yi kuka, ta ce "Ina da 'test' yau, kuma jibi za mu fara jarrabawa, kuma Yaya Habibu ya sani, yaya yake so in yi?" Dina ta ce "Hakuri za ki yi, haka Allah Ya shirya miki. Wani hanin ga Allah baiwa ne". *** J irginsu ya sauka a Abuja karfe biyar na asubahi. Ban da kunci da kumburi ba abin da Mairo ta ke yi. Dina sai lallabata ta ke tana ba ta hakuri. Idan takaicin ya yi takaici, sai ta kai hankici ta tsane hakwayen da ke 'racing' a fararen kundukukinta. Idan Dina ta ce "Ki yi wa Allah Mairo ki yi hakuri..." Sai ta ce "Haba Aunty Dina? Shekaru biyu ina wahala, in fadi, in tashi amma ace sun tashi a banza?" Wani farin dattijo, dan kimanin shekaru sittin da biyar, wanda alamun jin dadi, tsantsar ilimi da gogewar rayuwa ya boye shekarun nashi. Sanye cikin kaftan na wata irin farar sassalkar shadda da akalla ta baiwa naira dubu dari baya, yana da tsagin biyu-biyu a gefen fuskarsa na Fulanin Gaya. Biye da shi escort ne har guda biyu cikin bakaken suit wadanda harsashi na kowacce irin bindiga ba ya huda su, sun maka 'dark-spaces' fuskokinsu kamar hadari, sabanin dattijon wanda kyakkyawar fuskarsa ke yalwace da ni'imtaccen murmushi wanda da alama tabbatacce ne akan fuskarsa cikin kowanne yanayi. Abin nufi, cikin halin bakin ciki da farin ciki, kwanciyar hankali da tashin hankali, wannan sassanyan murmushin ba ya gushewa daga fuskarsa. A takaice dai na halitta ne, watau 'nature', shi ne a gaba wajen tarbar su Habibu a baya. Don haka kwarjininshi da haibarshi ya sanya dole Mairo ta daina kukan da ta ke, ta tsugunna har kasa ta gaida shi. Ya dora hannun damanshi a kanta ya ce "Barka da zuwa Maryamu. Godiya ga Allah da Ya sauke ku lafiya". Yaya Habibun kuwa ko arzikin kallo bai samu ba, sai matarshi ke binshi da kallon mamakin muguwar zabgewar da ya yi cikin kwanaki biyar kacal. Mairo ta sha mamakin ganin 'chebrolit' yau a gida Najeriya. Motar da ko a America, sai wanda ya ci ya tada kai. Ba wannan ne kadai ya razanata ba, sai tangamemen 'gate' irin wanda ake kira 'Mahdi ka-ture' da aka wangame musu a lokacin da motarsu ta sawo kai cikin unguwar Asokoro. Ta hango wani irin ‘American billa’ mai kama da jirgin ruwa. Ita dai Mairo ido ne nata, sai kuma ta cilla kafa duk inda ta ga an cilla. Tana cewa a ranta, watakila Yaya Habibu siyar da mu zai yi. Dama ni kudin nan nasa ai ban yarda da su ba. Sai dai kuma babu dar ko tsoro ko yaya cikin kalbinta, wadda ke cike taf da takaicin rabota da karatunta da aka yi babu gaira babu dalili. A kofar wani kayataccen falo mai kofar gilashi Yaya Habibu, dattijon da sauran mutanen da ke take mishi baya suka tsaya. Su kuma aka sa wata mace wadda ga dukkan alamu mai aiki ce, ta yi musu jagora cikin gidan. Ta nuna musu dakin da za su sauka, sannan ta sanar da su cewa, matar gidan tana asibiti, idan sun kimtsa su danna 'bell' za a shigo musu da abinci. Dina ce ta amsa, amma Mairo ta zama hoto. Dina ce ta fara yin wanka, sannan Mairo. Suka dauro alwala suka bada faralin sallar subhi da ta riske su a jirgi. Suka shirya tsaf, Mairo cikin 'swiss lace' ruwan madara da yarfin kananan duwatsu, riga da 'wrapper zani', ta yi 'simple' nadin kallabi a kanta. Dina cikin atamfar 'super' shudiya ita ma riga da zani da yalwataccen mayafi. A tsaitsaye suka ci abincin sabida kiran Yaya Habibu cikin wayar Dina cewa, su fito za su wuce asibiti. A babban asibitin koyarwa na Abuja, ita Mairo ta sha wajen matar gidan suka zo da ta ji an ce tana asibiti, sai raba ido ta ke cike da son ganin wace ce mamallakiyar wannan 'bungalow' din. Wanda aka yi amfani da hikima, ilmi da tunani wajen sarrafa shi. Kai ita a iya yawonta cikin U.S ba ta taba ganin irin wannan ginin ba, wanda ta fahimci cewa gidan wannan farin dattijon ne, da ya je tarbo su filin jirgi. Dattijon ne a gaba, sai 'escort' dinshi, sannan Habibu da Dina biye da shi, Mairo ce karshen shiga dakin, wanda ya kasance 'amenity'. Sabida cikowar da dakin ya yi da kyawawan mata masu kama daya, kuma masu kananan shekaru akalla daga mai talatin sai mai kasa da haka, sai kuma 'yammata tsararrakinta, wadanda ga dukkan alamu ko auren fari ba su yi ba, ta rasa inda tasan fuskarsu kamar ta sansu a wani wuri. Daga can gefe wata dattijuwa ce kyakkyawa cikin kyakkyawar suttura zaune bisa darduma, ta yi nisa cikin sujjadarta ba ta san me ake a dakin ba. Cikowar da dakin ya yi, shi yasa Mairo ba ta yi nasarar hango 'patient' din ba, wanda ke ta kelayo aman jini, har da guda-guda. Daya daga cikin matan ta rike shi tana kuka, sauran ma duk sharar hawaye suke yi da gefen mayafansu, wanda ke nuni da cewa kauna ce mai tsanani tsakaninsu da dan uwansu. Da sauri dattijon ya karasa gaban gadon ya tallafe shi cikin kirjinsa. Ya danna wani abu, da gudu likitoci biyar suka shigo. Nan suka yi umarnin kowa ya fita. Mairo dama tana bakin kofa, don haka ita ce ta farkon fita. Dattijiyar ma tana sallarta ko dagowa ba ta yi ba, su ma likitocin ba su ce ta fita ba. Daga likitocin sai dattijon sai Habibu, wanda idanunshi suka kada suka yi jajur, zaka iya hango tsabar tashin hankalin da ke kwance cikinsu. Don ma yana dauriya ne, amma da fashewa zai yi da kuka. Cikin gaggawa kowannensu ke ba shi taimakon da zai iya. Masu jona abin janyo numfashi na yi, masu auna bugun zuciya na yi, da ya ja wata doguwar ajiyar zuciya su dukka suka kalli juna suka girgiza kai, sannan suka ci gaba da aikinsu cikin kwarewa da sanin makamar aiki. Kafin su cire 'odygen' din su yi wa Habibu da dattijon alamar su biyo su ofishinsu. Fitarsu ke da wuya leburori suka shiga dakin suka soma tsaftace wajen. Har zuwa wannan lokacin dattijuwar nan ba ta daina sallah ba. Ba ta daina kai goshinta gaban mahaliccinta ba, domin ta yi imanin Shi kadai ne zai tashi kafadar danta, amma ba wadannan tarkacen nasaran ba. A can ofishin Dr. Fredrick Engles (consultant) na bangaren zuciya, bayani yake musu dalla-dalla na bugun zuciyar ba-zata da 'patient' dinsu ya samu, wanda ya yi mugun yi wa zuciyarshi illa farat daya. Ciwon zuciya na lokaci daya ya yi mishi mugun kaye, wanda idan ba a yi gaggawar magance mishi damuwarshi ba, daga yanzu zuwa kowanne lokaci komai zai iya faruwa. Ya kare da tambayarsu, shin ko sun san hakikanin abin da ke damun mara lafiyan? Domin su sunyi-sunyi ya fada musu, amma ya ki cewa komai. A nan ne dattijon ya soma yi wa babban likitan bayanin duk abin da Amirun ya fada mishi ranar da ya dawo, kafin ciwon ya ci karfinshi. Wato kanwar Habibu yake so, ita kuma ta ce ba zata aure shi ba. Habibu kuma ya dubi likitan ya ce "Ni kuma na yi alkawarin zan aurawa Amiru Mairo, ko da a gobe ne, idan hakan shi ne zai zamo FANSA ga lafiyarshi. Ko da kuwa ace wannan shi ne abu na KARSHE da zan gabatar a rayuwata". Dattijon ya ce, "A'a Habibu, ba za a yi haka ba, a bi-ta a hankali, domin dai da na kowa ne, ban yarda a tursasata bisa abin da ba ta so ba". Dr. Fredrick ya ce "Yanzu ina yarinyar?" Habibu ya ce "Tana waje, sun zo tun dazu. Sai dai ba tasan abin da ke faruwa ba. Da kyar ma idan tasan Amirun ne kwance a gadon asibiti". Likitan ya ce "A kirawo ta". Habibu ya fita, jim kadan suka shigo tare da Mairo, duk da ranta a bace yake, amma ba zaka karanci hakan a fuskarta ba. Ta nemi kujera gefen Habibu ta zauna, kanta a sunkuye, Dr. Fredrick ya yiwa su Habibu alamar su fita, yana mai ci gaba da rubuce-rubucensa cikin 'file'. Ofishin ya rage daga shi sai Mairo, har zuwa lokacin bai gama rubutun da yake yi ba. Daga bisani ya dago, ta karkashin farin gilashinsa yake kare mata kallo. Cikin ranshi ya ce, Dole maza su kwanta ciwo. Ya yi gyaran murya, sannan ya yi murmushi, ya ce "Maryam". Ta dago a hankali ta dube shi cikin fararen idanunta ba tare da ta ce dashi komai ba. Ya mike zuwa dan karamin firij da ke gefenshi ya fiddo gorar ruwan (Faro) ya bincire murfin ya sha, ya maida robar. Maimakon ya koma mazauninshi, sai ya ja kujerar da ke fuskantarta ya zauna. Ya sake yin murmushi kafin ya sake kiran sunanta. Wannan karon kam ta amsa, ta ce "Na'am". Ya ce "Sunana Dr. Fredrick, ni ne likitan da ke kula da lafiyar iyalin ABDURRAHMAN GAYA. Ina so ki ba mu hadin kai mu ceto rai, wanda ke cikin halin ha'u'la'i akan soyayyarki. Shin za mu samu wannan taimakon Mairo?" Cikin murya mai sanyi ta ce "Ni Doctor?" Ya ce "Ke fa Maryam". "Ta ya ya zan taimaka?" "Ta hanyar tayamu jinya, har sai ya samu lafiyarshi, domin a halin yanzu ba ya bukatar komai Maryam, sai soyayyarki, sannan ne mu ma za mu samu namu aikin ya yi kyau. Mai zai hana ki yarda ki auri mai sonki Maryam? Har ya ke neman rasa kyakkyawar rayuwarshi a dalilinki?" Cike da matsanancin mamaki ta ce "wai wanene?" Yayi murmushi ya ce "Taso mu je". Dr. Fredrick ne a gaba, Mairo na biye da shi. Ya tura kofar dakin dazu ya shiga, ita ma ta sa kai. Dakin babu kowa, sai mara lafiyan, wanda ke barci sadidan. Sai dai fa da ganin irin barcin da yake yi kasan ba na Allah da Annabi ba ne, na karfin allurai ne. Ba karamin bugawa zuciyarta ta yi ba (kamar wancan lokacin da ta fara ganinsa) a lokacin da ta sake yin arba, da dan Abdurrahman Gaya. Sai dai fa wannan Amirun ya sha ban-ban da wanda ta gani satittikan da suka gabata, ma'abocin kuzari da koshin lafiya, hadi da wasu nasibobi da ba duk maza Allah Ya mallakawa ba. Wannan Amirun ya rame fiye da tunaninta, sannan ga dukkan alamu ba karamin jin jiki yake yi ba. Ta tsaya jikin gadon kawai ba ta ce komai ba, sai dai zaka iya karantar karyewar da zuciyarta ta yi, hadi da tausayi tsantsa, da shi ma ya bayyana bisa kyakkyawar fuskarta. Tambaya ta ke cikin ranta, ita kuwa wace ce da Amiru zai kwanta ciwo a dalilinta? Kamar an ce da shi bude idonka, a hankali ya ke bude idonshi a kanta. To ita ma din kallonshi ta ke, sai ya dauka ko mafarki ne da gizon da ta ke mishi dare da rana, don haka ya dauke kanshi daga kanta, don bai gasgata idanunshi ba. Ya mayar da su kan Dr. Fredrick, wanda ke ta murmushi. Shi kam al'ummar Hausa suna ba shi mamaki akan soyayya, shi wallahi har duniya ta nade, bai ga macen da zata kwantar da shi a gadon asibiti ba. Balle mutun irin Amiru, dan gata gaba da baya, wanda duk irin macen da yake so a duniya zai iya aura. Ganin abinnasu yake kamar irin a fina-finan India. Ya kama hannun Amirun yana murmushi, ya ce "Kana da bakuwa fa? Wadda tayo tattaki tun daga U.S domin ta duba jikin ka!" Bai juya ya kara kallon Mairon ba, wadda ganinta ya kara haifar mishi da faduwar gaba. Kirjinshi in banda bugawa ba abin da yakeyi. Zuwa yanzu ya yarda ita din ce, ba gizo idanun shi ke mishi ba. Likita ya kama hannun Mairo ya dora mishi kan kirjinshi, dai-dai santar zuciyarshi. Tana jin yadda zuciyarshi ke bugawa fat-fat-fat! Amma don karfin hali bai fasa magana ba cikin nishi. "Ba wajena ta zo ba, ta biyo bayan Yayanta ne". Mace mai rauni da saurin karaya, sai ta soma kuka. Tun fil'azal Mairo mace ce mai tausayi, abin kuka bai da wuya a gurinta, bare an ce a dalilinta ne Amir ya kamu da ciwon zuciya. Wato wannan ne dalilin Habibu na yanke mata karatunta, Allah sarki Yaya Habibu, a da har ta kullace shi tayi fushi dashi mai tsanani. Ban da abinsu ita wace ce? Da kasancewarta tare da shi zai sa ya samu sauki? Likita ya daga mata gira, ya rausayar da kai, ta gane yana lallaminta ne ta rarrashi Amiru. Ta janye hannunta daga kirjinshi, cikin sassanyar murya ta ce "Ni na fada maka cewa ba wajenka na zo ba?" Ya lumshe ido a hankali, tsayin mintuna biyu bai bude ba. Dr. Fredrick ya zame ya fita, don ya lura Amirun ba zai iya yi mata magana ba idan yana kallonsu. Ya sake bude ido a hankali ya dubeta, da wani irin sassanyan kallo. Ta yi hanzarin sunkuyar da kanta, sabida wasu irin allurai da ta ji suna bin jinin jikinta. Hawayenta na diga a kasa dis-dis. Ya tara hannu ya taro hawayen, ya ce "Wannan hawayen kuma na mene ne? Ni da kika ce ba kya so na? Ban yi kuka ba, sai ke?" Muryarshi bata fita sosai, ba don tana kusa da shi sosai ba, da ba zata ji shi ba. "How dare you want to me to believe you (ta yaya kike so in yarda da ke cewa) kin zo sabida ni ne? Bayan kin fada min ga wanda kike so, ni ba kya so na? Na hakura na tafi, don me Habibu zai takuraki ki biyo ni? To me kika zo ki yi min? Kin zo ne ki kara min ciwon, ko kin zo karasar da ni zuwa kushewata ne?" Ta dago sosai ta dube shi, ya yi saurin kauda kai, don ba zai iya jurar kallon tsakiyar idanunta a wannan lokacin ba, wadanda suke kamar 'magnet' cikin nashi idanun, suke kuma sanyaya mishi zuciya, tare da karya karfin zuciyar duk da yake rikewa da jarumtar zucin duk da yake takama da ita. Har yake ganin zai iya jayayya da ita, ga shi tun ba a je ko'ina ba, ta fara karya lagon zuciyarshi. Ta ce a sanyaye "Har airport na bika, dai-dai lokacin da jirginku ya tashi. Ban ce lallai ka yarda da ni ba, amma Allah shaidata ne!" Ta juya zata fita, har ta kai bakin kofa, ya tattara iya sautin da ya rage mishi a makoshi ya ce "Mairo!" Ta dakata, hannunta jikin marikin kofar, amma ba ta juyo ba. Ya yi tari kuful-kuful! sau uku, kamin ya ce "Fushi kika yi? Za ki sake tafiya ki barni? Ciwon sonki ya karasa ni? Ki yi hakuri idan na fadi wani abu wanda ya bata miki rai, zafin sonki ne ya kawo hakan. Dawo ki zauna tare da ni, ina jin wani sanyi cikin zuciyata, a dalilin tsayawarki tare da ni. Ki yi wa Allah, kada ki sake barina, har zuwa karshen rayuwarmu. My life has no meaning…... Idan na rasa soyayyarki. I’m impotent….idan ba tare dake ba! Bana son Habibu ya takuraki ki aure ni, soyayyarki na ke nema, ba da tursasawar wani ba". Wannan lokacin ba ta ce komi ba. Ta rasa abin da zata ce, ta kasa tantance shin abin da ta ke ji game da Amirun cikin zuciyarta da illahirin gangar jikinta a halin yanzu, soyayya ce ko kauna ce? Idan kauna da soyayyar ne baki daya, to shi kuma Uncle Junaidu fa? Shi kuma me ta ke masa idan ba so da kauna ba? Idan haka ne ke nan MAZA BIYU ta ke so ko yaya ne? Soyayya guda daya ce, wadda a halin yanzu ba ta san ko ta waye ba, don haka ba zata ce ba. Amma data tuna halin da Amirun ke ciki, yana bukatar lallashi da kauna daga gareta a daidai wannan lokacin kamar yadda likitanshi yace, sai ta dawo kujerar da ke fuskartarshi ta zauna kanta a kasa. Kamun kai da kunyar Mairon, su ne manyan al'amuran yarinyar da suke kara masa kaunarta. Ya tabbatar ba zata taba bude baki ta ce, tana sonshi ba, sai dai idan su kwana a hakan, wannan din ma ba karamin burge shi ya yi ba. Domin duk yarinyar da zata budi baki gatsar ta ce da namijin da bai zamo mijinta ba, ina sonka. To wallahi ba matar aure ba ce. Inda Allah Ya ceceta daga kaifafan idanun Amirun, shi ne shigowar Yaya Habibu, Dr. Fredrick da dattijon da a yanzu ta gane shi ne Alh. Abdurrahman Gaya. Mahaifin Amiru. Cikin murmushin jin dadin ganin dan nashi cikin yanayin da ya bashi mamaki, zaune sosai bisa gadon ya zuro kafafunshi kasa. Fuskarshi cike da walwala da yalwataccen murmushi ya karaso gare su, shima Amirun murmushin yake yi. "A'ah sauki ya samu, lallai, kai Mairo ta iya jinya!". Amiru ya harare ta, ya ce "Ni ba wani jinyata da ta yi, sai kuka ta ke yi mini. Kai Yaya Habibu mai yasa ka takurata ta zo? Me ya hada ciwona da zuwan Mairo Nigeria? Alhalin karatu take yi? Da ka kyale ta ai zan samu sauki ne a hankali cikin yardar Allah". Habibu ya harare shi ya ce "Kwarai fa, shi yasa na ga kamin ta zo ana ta janyo maka numfashi". Duk suka yi dariya ban da shi Amirun. Da kalaman Habibu suka jefa shi a tunanin anya ya cika namiji? Anya shigowar Mairo rayuwarsa bata maida shi mace ba? Dr. Fredrick ya ce "Ya ci abinci Mairo?" Ta girgiza kai, sannan ta dubi kular abincin da ke kan lokar jikin gadon, ta dauko ta bude, farfesun kaza ne da ya ji kayan kamshi, a daya kular 'chips' ne da soyayyen kwai. Tana son ta tambaye shi wanne zai ci a ciki, amma kunya ta hana ta, don haka ta zuba kowanne kadan cikin faranti daban-daban ta mika mishi. Dai-dai sanda ya debo shanyayyun idanunshi ya dora a kanta, sannan ya mika hannu ya karba. A hankali ta ce "Ba zaka wanke baki ba?" Cikin kankanuwar murya shima ya ce "Kin bani abin wanke bakin na ce ba zan wanke ba?" Ta ce "Ai ban san inda ya ke ba". Alh. Abdurrahman da kansa ya bude lokar ya fiddo sabbin burushi da makilin ya mika mata, ta bude ta shafa jikin burushin, Yaya Habibu ya mika mata roba. Tana zuba mishi ruwan robar 'swan' yana wankewa har ya gama, sannan ya soma cin abincin. Shi kanshi likitan ya yi mamakin yawan abincin da Amiru ya ci, wanda tunda aka kawo shi sai yau ya ci, “lallai so ba dama”. (Ya ce a zuciyarshi) sai ruwa ake kara masa mai dauke da sinadaran abincin maras lafiya. Hajiyar Amiru ta shigo, bakinta ya kasa rufo, ganin Amirunta na cin abinci, alamun sauki sun bayyana sosai a gare shi. Ta ce "Kai masha'Allah, har abinci ake ci? Lallai sauki ya samu (don ita ba ta san musabbabin ciwon Amirun ba)". Ta kalli Mairo da fuska ma'abociyar walwala, ta ce "Ina muka samo 'yar kyakkyawar budurwa?" Mairo ta dukar da kai, Alhajin ya ce, "Kanwar Habibu ce, kuma surukarki insha Allahu". Murmushinta ya fadada sosai zuwa dariya, ta ce "Da gaske?" Ta juya ta kalli Habibu "Na ce da gaske ne Habibu?" Ya yi murmushi ya ce "Idan Allah Ya yarda". Kunya a wajen Mairo, kamar ta nutse cikin kasa. Hajiya A’isha ta kamo hannunta ta rike cikin nata cike da matsananciyar kauna da kulawa. Ana haka Dina da wasu daga cikin kannen Amiru suka shigo, don haka dakin ya yi albarka, ba masaka tsinke, wanda ke nuni da lallai Amiru dan dangi ne. Kowa na fadin albarkacin bakinshi. Akan yanayin jikin Amirun. Ba su bar asibitin ba sai dare, aka barshi da Habibu wanda shi yake kwana da shi. *** 8/5/21, 3:11 PM - Kawata: D Awashegarin daurin aure, wato lahadi, tun safe motocin daukar amarya zuwa garin Gaya suka iso. Dina ta shirya amarya cikin fararen liffaya na Larabawan Mouritania, ta fesheta da turarukan 'gibenchy' su Habiba da Hajara suka sanyata a tsakiya, Dina na gidan gaba suka nufi garin Gaya. Anyi musu tarba ta GIRMA, a gidan sarkin Gaya na lokacin, wanda ya kasance kaka ga Amiru, tunda kuwa shi ya haifi Alhaji Abdurrahman, dangin Mairo sun tabbatar Mairo ta yi aure da dan dangi, wanda ake so, ake kauna kwarai, ake kuma son abin da yake so, sannan aka san mutumcin dan Adam. Kwanansu uku ana shagalin biki irin nasu na masarautar Gaya, kuma fulanin usli. Mai martaba Sarki Abdulkarim Sarkin Gaya III ya yi wa amarya kyautar bajimai uku da sabuwar mota. Washegari suka nufo Abuja inda aka shiryawa amarya gidanta cikin gidan surukanta, bangare guda, wanda dama tun sanda za a gina gidan an gina shi ne musamman sabida Amirun. Duk da dai gidan ba ya bukatar komi, wannan bai hana Habibu da Alh. Abbas yi wa Mairon su gata ba. Dakuna uku manya-manya aka ba su suka shakewa Mairo da dukiya. Sai dai fa ba wai rambatsau ba, a'ah, komi ya dace da muhallinshi. Cikin tsari mai burgewa da ban sha'awa, sannan sun kawota da gararta (trailer) guda. Lokacin da suka shigo wajen Hajiya Aisha aka fara kai Mairo, inda dukkan dangin ango suke tare da Hajiyar a babban falonta. Duk kannen Amiru guda goma sha biyu na ciki da na waje sun hallara, suka karbi amaryarsu cikin mutuntawa da kamala. Daga nan sai sassan Daddy wanda ya dade yana yi musu addu'a ta neman dacewa a duniya da lahira. Daga nan aka taho da amarya bangarenta banda kuka da shessheka ba abin da ta ke yi. Ta kama Dina ta rike tamau, ta rantse ba zata tafi ta barta ba, sai dai su koma tare. Dina na dariya ta ce "Ina kika taba jin anyi haka Mairo? Ai auren ke nan, YAKIN MATA…… Ko ba ki ganin nima namu gidan na baro na ke zaune da Yayan ki, a inda ba ni da kowa? Ke kuwa fa? Ga ki ga su Hajiya, ga su Amina, ko su kadai sun isheki debe kewa. Duk lokacin da kike son zuwa Kano za ki je". Cikin kuka ta ce "Yanzu Aunty Dina ni da ku shi ke nan? Ni da su Little Mairo shi ke nan? Sannan ba zan koma makaranta ba?" Dina ta ce "Idan na ce za ki koma makaranta, ko ba zaki koma ba na yi karya, sabida a halin yanzu ba mu da iko da ke, sai abin da mijinki ya hukunta a gare ki. Yara kuwa na yi miki alkawarin da zarar sun samu hutu zan kawo miki su. Ki kwantar da hankalinki ki zauna da mijinki Amiru is a nice person". Sabah ta yi murmushi, ta ce "Sai ma kin zauna da shi for a little while..." Dina ta ce "To kinji ba, kannenshi ma sun shaida". Wayarta ta hau ruri ta yi murmushi "Ni ma nawa tsohon angon kirana yake yi in mishi tausar gajiyar da kujuba-kujubar aurenki ya sanya shi. Don haka amarya sai ince, asubah ta gari". Tana ji tana gani Dina ta fice, ji ta ke kamar ta dora hannuwa aka ta ce "Wayyo Allah". Ko ta sami sa'idah. Ya rage daga ita sai su Amina, don su Hafsat kannen Dina duk sun tafi tun dazun. Nabilah dama ba ta taho Abuja ba, daga Gaya suka nufi gida ita da Isma'il. Suna so ta yarda su yi hira, amma amaryar tasu ta ki sakin jikinta. Ganin abin ta ke kamar a mafarki, wai yau ita ce a gidan wani mijin ba Uncle Junaidu ba. Ta yi saurin yin istigfari da wannan mummunan tunanin ta amince, ta yarda da kaddararta. Ta amince haka Allah Ya rubuta musu dukkaninsu. Zata koyawa zuciyarta juriya da karbar rayuwa a duk yadda ta zo mata. Hajiya ta yi kiran wayar Amina, ta ce duk abin da suke yi su bari su taho gida haka dare ya yi. Dukkansu suka mike suna yi mata sai da safe Hajiya na kiransu. Ta rike mayafin Sabah tana kuka sosai har ta karyawa Sabah zuciya, ta ce su tafi zata taho. Ta koma ta zauna ta ce "Haba Antinmu? Ya ya kike abu kamar karamar yarinya ne? Amare yanzu ba sa kuka, sakin jiki suke a sha soyayya. Kuma ni kinga idan ban tafi ba zan yi laifi wurin Hajiyarmu, don haka ki yi hakuri na tafi na yi miki alkawarin gobe da safe zan dawo idan Allah Ya kaimu". Haka ta kalallameta da dadin baki ta samu ta gudu. Ya rage sai Mairo kadai cikin katafaren gidanta, daga ita sai halinta. Ji ta ke kamar an kawo ta kabarinta. Don haka ta ce bari kawai ta yi ibada ko ta samu sanyin zuciyarta. Ta mike a hankali, ba tare da ta ajiye nadin laffayar da ke jikinta ba. Ta nufi kofar da jikinta ya ba ta bandaki ne, ba don ta saba da ire-iren wadannan wuraren ba, da hakika ta tsaya kauyanci. Komi na bandakin wanda ya kasance (Jacuzzi) kalar ruwan hoda ne, watau 'pink' kamar yadda makeken bed room din shi ma ruwan hodar ne da ratsin fari. Ta dauro cikakkiyar alwala ta fito. Ba tare da ta tsaya neman darduma ba ta nemi wani gefe a can wani korido na dakin ta tada ikama. Sallolin neman biyan bukatar duniya da na lahira da neman dacewa a rayuwar aurenta ne ta ke yi. Cikin sujudunta tana mai yi wa Babanta da Innarta addu'ar samun rahma da gafarar Ubangiji. Cikin tahiyarta ta ji alamun ana taba kofa, kafin cikin nutsuwa ta ji an murda kofar an shigo. Angon ya bayyana a dakin cikin fararen kayan barci. Dai-dai lokacin da ta yi sallah ta mike ta kara tada sallah, ya aje kwali da tambulan din da ke hannunshi, shi ma ya shiga ya dauro alwalar ya cimmata suka ci gaba da sallar tare. Agogon bango ya buga karfe biyu dai-dai na sulusin dare lokacin da kowane mai rai yake neman hutu, amma ga wadannan ma'auratan abin ba haka yake ba. Sun fada wata duniyar tunani ta daban, ba wannan tamun wadda muke ciki ba. Abin nufi, kowanne da tunanin da ke cin ranshi. Ba auren sha'awa ya yi ba, auren so da kauna ya yi. Don haka babu sha'awar Mairo ko yaya a tare da shi a daren yau. Ya dauko kwalin 'fresh milk’ na madarar 'oldenburger' da ya shigo da shi ya tsiyaya a kofin ya mika mata. Ba tare da ta tashi daga inda ta yi sallar ba, ta mika hannu ta amsa. Ya sauko daga gefen gadon ya yi zaman rakuma a gabanta. Ya dauki dukkan hannuwanta ya rike cikin nashi. Wannan ya haifar da tashin tsigogin jikinta duka a lokaci daya. Ta samu kanta cikin matsananciyar sha’awar mijinta Amiru, wanda sassanyan kamshinsa na turaren 'Miyaki' ke kara dagula mata al'amura, dama yaya lafiyar kura, balle an tsokaneta, amma ga shi Amirun, abin ba haka yake ba. Zuciyarshi ta kasa amincewa Mairo na sonshi, a ganinshi Habibu ne ya takurata ta aure shi, don haka akan me zai sallama mata soyayyarshi? Yana son ya koyar da ita sonshi da kaunarshi, ba wai sha'awarshi ba kamar yadda ya karanto karara cikin fararen kwayar idanunta. Haka suka yi ta zama dungur-gur bisa kafet har aka yi kiran assalatu, kowanne na ji da miskilanci. An rasa wanda zai fara keta billensa, ya kwantar da kai ga dan uwansa. Ya rausayar da kai, ya ce "Mu je mu sake alwala". Ba musu ta mike domin dama ta tsauwala da wannan zaman na babu gaira babu dalili. Don haka koda suka idar da sallar Mairo gefen gado ta koma ta takure. Shi kuma ya ja filo ya jefa bisa kilishi ya kwanta. Ta leka ta hango idonshi a rufe ta dauka barci ne ya dauke shi, don haka ta mike ta warware laffayarta, yadda zata ji dadin yin barci, ta nade a gado ta ja bargo ta rufa. Wani irin fitinannen barci na fizgarta, hakan yasa ba da dadewa ba sarkin barayin ya yi awon gaba da ita. Mairo ba ita ta farka ba sai wajejen karfe goma na safe. Shi ma din sakamakon feshin ruwan da ta ji akan fuskarta ne. Ta juya a hankali saitin da feshin ruwan ya ke, Amiru ne ke taje sumarshi. Ya yi shiri cikin bakaken 'suit' masu ban sha'awa. Ta zuba mishi ido kurr kamar mayya, har yawun bakinta na tsinkewa, sakamakon wata matsananciyar sha'awarshi da ta kara saukar mata. Wannan mutum kamar Romeo ya ke, kamar an ce da shi 'juya' ya juyo suka yi ido hudu da ita, ya daure fuska sosai, ya ce "Lafiya kike kallona? Ko na yi kama da tsohon saurayinki ne mai sunan aljanu? Haka kawai yarinya kin zama kurma, in dai ni ne to mu zuba, shege ka fasa". Ya kuta, ya sake cewa "Halan Dina ko gayar da mutane ba ta koya miki ba?" Ta dauke kai ba ta ba shi amsa ba, sannan ta yunkura ta mike ta fada bandaki ta yi wanka tare da wanke baki ta fito. Yana tsaye jikin sif dinta yana amsa waya, ga dukkan alamu da Harrit yake wayar, wani kululun bakin ciki ya taso ya tokare ta. Ta yi saurin komawa bandakin don ta dauka ya fita ta aje tawul din ta maida kayan jikinta. Ta sake fitowa wannan karon ya gama wayar yana sanyata a aljihun wandonshi. Ya bi-ta da wani irin kallo kasa-kasa ya girgiza kai, ya fita yana cewa "Abinci za mu ci, ko yau ma ba za a ci da ni ba?" Ko ta tafas ba ta ce masa ba, don ta lura neman baki yake yi da ita. Ta shirya cikin shadda 'orange' babbar riga 'senegalese', ba ta yin kwalliya rankacau don haka kullum fatarta ta ke danya shar (fresh). Ba kankanuwar yunwa ta ke ji ba, don haka ta nufo falon ta cimmashi a 'dinning area' na falon. Kallo daya ya yi mata ya dauke kanshi, zuciyarshi na bugawa. Wannan yarinya kamar Juliet ta ke. Ta ja kujera mai fuskantarshi ta zauna, sannan ta fara bude ma'adanan abincin, sinasir ne da waina, sai hadaddiyar miyar agushi wadda ta ji naman rago, a gefe farfesun hanta da Koda ne sai Shawarmah da snacks dangin su meat-pie, samosa, spring rolls da sauransu. Cikin sassanyar murya ta ce "Can I serve you?" Hakika ya ji wannan muryar har cikin kokon ransa. Bai iya ya amsa ba, illa kai da ya gyada mata, don haka ta fara da hada mishi ruwan 'lipton' mai zafi da ganyen 'Hemorrhoid tea', sannan ta zuba mishi Sinasir din da farfesun a faranti daban-daban. Ya yi mata wani sassanyan kallo ba tare da ta sani ba, sannan ya soma ci. Ta hada 'lipton' ta sha, amma ta yi-tayi ta ci abinci a gabansa ta kasa. Ta mike ta ce "Zan shiga wajen Hajiya". Ya ce "A'a, sai kin ci abinci na gani tukunna". Ta koma ta zauna, ta dauki sinasir guda daya, ta sanya a faranti ta soma ci cike da kunya. Ya tura mata farfesun gabanshi ya ce, "Cinye shi". Ba musu ta karba don ba zata iya yin jayayya da shi ba. Sai da ya tabbatar ta cinye, sannan shi ma ya mike yana cewa "Mu je na rakaki wurin Hajiyar". Tare suka jera har gidan Hajiya. Tana sallar walha sanda suka shiga a karamin falonta. Sai da ta idar ta shafa addu'o'inta sannan ta juyo gare su, cikin matsananciyar kauna ta mikawa Mairo hannu "Zo dawo nan kusa da ni diyata". Sai ga su Sabah su ma sun fito, suka gaida Yayansu wanda ya maida hankali ga amsa kiran da ke shigowa cikin wayarshi. Daga karshe ma fita ya yi ya barsu, bayan ya fadawa Hajiya zai je ya raka bakinshi airport. Su Amina kamar su hadiye Mairo. Nan ta wuni sur tare da su. Bai dawo ba sai bayan la'asar, lokacin da ya shigo tana kicin ita da su Sabah suna hada abincin dare. Hajiya na falo ta ce "Sai yanzu?" Ya ce "Wallahi kuwa, ai bakin nawa ne suna da yawa, kuma jirage daban-daban za su shiga, amma dai alhamdulillah duk sun tafi sai fatan Allah Ya sauke su lafiya". Hajiya ta kwalawa Mairo kira, ta fito ba tare da ta iya hada ido da Amirun ba. Wanda ya bita da kallo kamar bai santa ba. Ta russuna gaban Hajiya cike da girmamawa, Hajiya ta ce, "Shi miji idan ya dawo yana bukatar kulawar matar sa, ta hanyar yi mishi sannu da zuwa, da ba shi abu mai dan sanyi ya sha kafin a gabatar mishi da abinci. Don haka bi shi ku tafi, su Amina za su shigo muku da abincin idan an karasa". Cikin jin nauyi ta ce "to Hajiya". Shi abin ma dariya ya ba shi, wai wannan katuwar ake koyawa kula da miji, Hajiya ba ta san yaran zamani da wayonsu ake haifarsu ba, balle Mairo rainon Dina, kula da miji sai dai ta koyawa wasu, sai dai in ba ta sa kanta ba. A 'bedroom' dinta ya cimmata, tana kokarin sauya kayan jikinta. Duk dauriyarshi da jarumtakarshi ya kasa sarrafa kanshi, don haka ya yi hanzarin komawa da baya ya ja mata kofar. Ta yi saurin juyowa amma ba ta ga kowa ba, sai karar rufe kofa. Ta ci gaba da abin da ta ke yi kamin ta jiyo sallamar Amina da Rayyah a falo. Ta fita suka aje abincin a 'dinning. Suka yi 'yar hira ba su jima ba suka fita. Ba ta san dakin da ya shiga ba, ko ta sani ma ba zata shiga ba, don haka ta zauna nan falon tana jiran shi sai zuba kamshi ta ke. Zamanta da wajen mintuna ashirin sannan ya fito, da alama wanka ya fito. Wannan karon cikin shigar kananan kaya, farar shirt din (Tommy Hilfiger) da bakin wando Tokyo. Sai ‘miyaki’ ke tashi. Mairo ta daga kai a hankali tana kallonshi. Wani irin abu na tsirgawa cikin jikinta yana tada tsigogin jikinta. Kallo daya ya yi mata ya karanto halin da zuciyarta da ma gangar jikinta ke ciki. Ya murmusa ya daga gira ta kara rikicewa, a ranshi ya ce "munafuka! Idan dai wannan Amirun ne yarinya, to kwalelenki har sai kin so shi, kin kaunace shi don Allah, tunda kiri-kiri kin fada mishi cewa ba kya sonshi, akwai wanda kike so, don haka wannan jikin ma da kike wa marmari ba zaki same shi ba". Abincin da Mairo ba ta iya ta ci ba ke nan, sabida gani ta ke kamar Amirun yana karanto zuciyarta. To da gaske hakan ne, tunda yake shi din ba yaro ba ne. Ya fita ilmi da hankali nesa ba kusa ba. A kwayar idanunta ya gama gane ta tsaf. Yana kallonta sai caccaka cokali ta ke cikin abinci ta kasa kai ko loma guda. Shi kuwa cin abincinshi yake cikin nutsuwa da kwanciyar hankali yana kallonta a kaikaice. Wani zubin ya yi murmushi, wani zubin ya girgiza kai. Wannan karon bai takurata da lallai sai ta ci ba, don ya tabbata ba zata ci din ba. Dan Abdurrahman Gaya, kadai ta ke so a jikinta. Kararrawar kofar shigowarsu ta yi kara, wannan ne ya ceci Mairo daga kaifafan idon Amiru. Da azamarta ta mike ta nufi kofar ta bude. Ta sha mamakin ganin Daddy da kansa. Cike da girmamawa ta ba shi hanya ya wuce. Sai da ya zauna a 'seater' ta zube a kasa tana gayas da shi. Ya ce "Yaya bakunta Maryamu?" Ta ce "Alhamdu lillah". "Babu wata matsala ince ko?" Ta ce "Babu Daddy". Amiru ya baro kujerarshi ya iso inda Daddyn ya ke ya zauna a gefensa suka soma hirarsu. Ta mike ta je kicin ta kawo mishi ruwan (Eva) mai sanyi da lemun 'shany' sannan ta gabatar mishi da abinci. A nan ne ya yi murmushi, ya ce "Lemun kadai zan sha Maryamu, na Hajiyarku yana can yana jirana, kada inci a wajenki inje in kasa cin nata". Ta yi murmushi ta ce "To Daddy babu komai". Ta koma daki ta barsu don su gana. Yau ma irin kwanciyar jiya suka maimaita, wato shi yana bisa kilishi ita tan kan gado. To haka kwanakin da suka biyo baya. Idan ka gansu a gaban Hajiya da Daddy. ko su Amina, ba zaka taba zaton cewa zaman 'yan Marina suke ba. Kowanne na ji da miskilancinsa ya kasa kwantar da kai ga dan uwanshi. Ga ita Mairo, a ganinta shi ne namiji, shi ya kamata ya nuna mata kulawa irin ta kowadanne ma'aurata amma ba ita ba. Sannan ba haka Dina ta gaya mata ana yiwa amare a renakun su na farko a gidan aure ba. Ba haka kuma ta ga Yaya Habibu yana yiwa Dinan ba. Amiru yace yana son ta baka da zuci, amma bayan aurensu ta ga ba haka ba. Wannan al’amari yana sanya ta cikin wani irin tunani mai zurfi da wuyar fassarawa. Har ta kasa jin dadin rayuwar gabadaya. Shi kuma Amirun, a nashi bangaren, ya riga ya saba samun tarairaya ta karshe daga banasariyar matarshi, kamar ta goya shi. Bai san cewa matar Bahaushe da matar bature akwai wasu manya-manyan banbance-banbance ba. Hakika mu Allah Ya ba mu wannan darajar ta kamun kai da alkunya, wanda ya zamo kowanne irin namiji, duk kyau, aji, mukaminsa da iliminsa dole ya lallame mu idan har yana son ganin yadda ya ke so. Yau juma'a ta tashi da kewar Dina kwarai a ranta, ba abin da ta ke so irin ta ji muryarta. Ya dawo daga sallar juma'a shi da Daddy daga babban masallacin Abuja kamar yadda suka saba kowanne sati idan suna nan. Ta rasa yadda zata yi ta roke shi ya ba ta aron waya. Dabara ta fado mata don haka ta nemo biro da 'yar takarda ta rubuta mishi, ta soke a jikin kofar dakin da ta tabbata shi ne nasa. Ya zo shiga dakin don sauya manyan kayan da ke jikinsa ya cimma sakonta. Ya yi murmushi ya sumbaci takardar ya share ta bai ce mata komai ba. Sai da daddare sun yi shirin kwanciya, bayan ya jefa filonshi ya mike. Ta zuba tagumi a gefen gado abin duniya ya dame ta, idan jurinta miskilanci ta gamu da wanda ya fi ta miskilanci. Ta juyo kadan, ga dukkan alamu barci mai nauyi ya tafi da shi. Cikin sanda kamar barauniya ta iso gabanshi don ta dauki daya daga cikin wayoyinshi sai caraf! Ya damke hannunta tareda wayar ya kuma bude lumsassun idanunshi sannu a hankali a kanta. Kunya ta duniya Mairo ta gama jinta. Ashe ba a yi komai ba sai sanda ya fizgota ta fada gaba daya a jikinshi. Ta rasa inda za ta sa kanta don kunya, fargaba da wani bakon tsoro da ya ziyarce ta duk a lokaci guda. Jikinta ya soma rawa kamar mazari, amma hakan bai sa ya cikata daga sassaukan rikon da ya yi mata ba. Duk yadda ya so da su hada ido cikin dan sauran hasken fitilar baccin dake dakin amma Mairo ta ki. Runtse idon ta shiga yi da karfi. Wani sabon Son mijinta AMIRU da kaunarsa ne farat daya suke tsirgawa a zuciyarta. Wadanda bazata iya tantance tun tsahon wane lokaci hakan ya soma ginuwa a zuciyarta ba. Yana danne wancan feeling din mai karfi da dukkan tasirin sa, wanda zuciyarta ta dade tana kallon Amiru dasu. Tareda gina mafarkanta da shi a kansa. Ya dago fuskarta daga kirjinsa, a wannan lokacin ya yi nasarar hango cikin kwayar idanunta, cikin murya irin ta wanda ya tashi daga bacci ya ce "Sata ko Mairo?" Ta ce "A'a, ina so in kira Anti Dina ne, kuma na fada maka ai ba ka ba ni ba". Ya ce "Ni ban kai kararki wajen Anti Dinan ba, sai ke za ki kai karata?" Kamshin 'mouth fresh' dinshi na fizgarta, yana sanya mata rashin kuzari ta ce, "Me ka yi min da zan kai kararka, kuma nima me na yi maka da zaka kai karata?" Ya ce, "Kin yi min laifuffuka da yawa Mairo, wadanda idan na fadawa Anti Dina sai ta zane ki wallahi". "Dame-dame ne laifuffukan nawa?" "Ai ba ki ma sansu ba?" "Da na sani bazan tambaye ka ba". "To sunkuyo nan na fada miki". "Kinga na farko ba kya gaishe ni da safe, sannan ba kya zuwa dakina taya ni kwana, sai dai ni na biyo ki dakinki. Sannan idan na biyo ki ba kya hada makwanci da ni, sai ki bar ni a kasa ki dare gadonki. Haka Dinan ta fada miki tana yi wa Habibu? Ko ba ki ga har kaya ita ta ke saka mishi ba? Amma ke bana jin ko inda nake wanka kin sani a gidan nan ko don har yanzu ba kya sona?" Taji zafi a ranta da kalamansa. Da zai taimake ta da ya daina zancen rashin so a tsakaninsu. Ta ce "Maganar ina sonka ko bana sonka, tunda mun riga mun kasance cikin inuwar AURE, to bata taso ba, bare kuma ni wallahi ban taba jin kiyayyarka a raina ba. Ko wancan lokacin da na fada, na fada ne kawai don ban amince da irin son da zuciyata ta ke yi maka ba". Ya lumshe ido a hankali, tare da sake yi mata muhalli cikin ni'imtaccen kirjinshi mai cike da gargasa. Yace “wane iri ne shi wancan son?” Ta dan rufe ido kafin tace “irin na shirme!”. “Wane irin so ne irin na shirme?” Amiru ya tambaya cikin mamaki. Mutsu-mutsun kwacewa ta hau yi, ko zai kashe ta bazata iya yi masa wannan bayanin ba. Sako riko ta yayi da karfin da yafi na dazu, ya juyo ta sannan ya sa hannu ya dago habarta. Yana iya ganin kyallin dake cikin idanunta wadanda ke cike taf! Da soyayyar data mamaye su. Soyayya mai cike da kauna mara algus or material attachement. Zaiyi rantsuwa bai taba ganin wannan yanayin cikin kwayar idanunta ba, wani yanayi da yake matukar jira, yake kuma da yakinin zai iya cigaba da jiran zuwansa cikin idanun Mairo har nan gaba da shekaru goma kafin ya yarda ya hada shimfida da ita. "To yanzu fa? Mairo! Mairo yanzun kina sona?" Amiru ya tambaya, da wata murya tamkar ba tashi ba. Sai ta yi murmushi, irin wanda bai taba gani bisa siraran labbanta ba. Wannan kadai ya tabbatar mishi da cewa, ya gama mallakar soyayyar Mairon, saura da me? A take shi ma ya soma mallaka mata ta shi. Cikin wani irin salo mai ban mamaki da Mairo ba ta taba tunanin akwai irin wannan soyayyar a duniya ba. Koda a duniyar karance-karancen novels dinta kuwa. Su Hajiya Mairo, tun ana dauriya, ana cijewa, cikin bin shawarwarin uwardakin ta Dina, har lissafin ya soma kwace mata......aka kai ga gejin kiran Anti Dinah, Baffa, da Yaya Habibu su zo su kawo taimako. Yau har Ladidi da Nabilah sun sha kira don tana ganin karshen rayuwarta yazo! Shi kanshi Amirun ya rasa control din kansa, ta yadda har zai yi tunanin cewa Mairon virgin ce, ba kamar matarshi ba. Tunda yake a rayuwarsa bai san akwai Hurul-eeni tun a duniya ba. Bai san aure iri-iri ne kuma suna ya tara ba. Don haka bai farga da aika-aikar da ya yi ba, sai da ya duba ya ga Mairon ta sume mishi. Ba ita ta dawo hayyacinta ba sai da sanyin ruwan 'ragolis' ya ratsa kwanyarta, da sauran sassan jikinta. Ya rungume ta sosai, tamkar ya tsaga kirjinsa ya sanyata, cikin shauki ya ce "Mairo kar ki gudu ki barni! Mairo ki ci gaba da zama da ni ko ba kya sona, ni ina sonki da dukkan ruhi na! Ki rike naki son ko bazaki bani ba! Zan zamo ‘impotent' a duk ranar da kika guje ni, ko kika juya min baya...!" *** MAIRO A GIDAN AURENTA! Zuwa yanzu, wato watanni biyu a gaba, Mairo an zama manyan mata, an iya komai na kula da miji. Ta iya daukewa mijinta lalurar da mata hudu ba zasu iya dauke masa ba. Soyayya, kauna da shakuwa ke kara kamari tsakaninta da mijinta. Ga kauna da kulawa da ta ke samu daga surukanta kamar su suka tsugunna suka haife ta. Cikin wannan dan tsukin Amirun ba ya samun zama sosai, sabida shirye-shiryen bude bankinsu da suke yi shi da Habibu. Shi Habibun ke tafiyar musu da komi ta can, shi kuma yake tafiyar da komi ta nan. Gaba daya ya mance da wata Harrit da ya sanya lambarta a (divert call), sannan a ka'idarshi bai daukar wayar da bai san lambar ba. Al'amuran gabanshi kadai sun ishe shi, sannan Mairon shi kadai ya sanya a gaba, a yadda yake ji cikin ransa, ta ishe shi rayuwar duniya da lahira. A wannan daren na ranar talata shiri yake don tashi zuwa Washington a washegari, domin mika takardar yin retire daga aiki a World Bank, a gefe guda kuma ga Mairo ta dira shagwaba ita dai sai ya tafi da ita ta ga Yaya Habibu da Dina. Ya kamo hannunta ya ce "rigimarki yawa gare ta Mairo, na fada miki Washington za ni ba Michigan ba. Kuma ba dadewa zan yi ba, karkari na yi sati biyu. Ina duba yiwuwar komawarki makaranta, idan komi ya dai-daita gidan Habibun zan barki ki zauna gaba daya". Ai da jin haka ta yi tsalle ta dane shi cikin nuna farin cikinta a fili. Inda shi kuma ya juyo ta gareshi ya bi ta da deep-kisses tsakiyar bakinta, wuyanta, da idanunta; mai nuni da cewa, lallai zai yi kewarta. Ita da Sabah suka yi mishi rakiya filin jirgi a asubahin washegari. A gaban Sabah ya rungume ta yana fada mata wasu irin kalamai masu rikirkita kwakwalwa cikin kunnuwanta. Sabah sai ta sa mayafinta ta kare fuskarta tana murmushi. A zuciyarta kuwa addu'a ta ke, Allah Ya ba ta miji irin Yayanta. Yana sauka a Washington ya tarar tuni Raymond da Franklyn suna jiran isowarshi, don haka suka zubo jakarshi a bayan mota suka nufo cikin gari. Kai tsaye gidanshi suka nufa suna tafe suna yi mishi bayanin muhimman abubuwan da suka gabatar (in his absence), ci gaban da aka samu da shortcomings din duk da ya biyo baya. Suna sanyo hancin motarsu a farfajiyar gidan ya ga bakuwar mota kirar (Ferrari 458) kusa da ta Harrit. Bai kawo komi a ranshi ba, don ya yi zaton baki ne Harrit din ta yi kasancewarta ma'abociyar hulda da jama'a, don haka ya yi amfani da mukullinshi ya bude kofar. Su Raymond suna daga waje suna magana. Ya ratsa falon babu kowa, ita ba musulma ba, balle ya yi mata sallama don haka kai tsaye ya sanya kai 'bed-room' dinsu. Idanunshi kuwa suka yi kyakkyawan gani. Harrit ce kwance tare da wani bature dan uwanta haihuwar uwarsu-ubansu cikin halin turmi da tabarya. Ya tsaya kawai yana kallon tashin hankalin da bai taba gani a rayuwarshi ba, wanda a take ya tabbatar ba komi ba ne, hakkin iyaye ne da son zuciya suka jawo mishi (al'ummar musulmi irin Amiru sai a yi hattara, kafiri har gobe kafiri ne, duk soyayyarsa gareka kuwa, kuma babu soyayya ta hakika tsakaninshi da musulmi sai yaudara da soyayyar manufa). Jikinsu ne watakila ya ba su ana kallonsu, su duka suka juyo a razane, amma abinka da nasara da babu digon kunya ko tsoron Allah a tare da shi, sai suma suka zuba mishi idanun. Ya yi saurin dauke idonsa ya fito falon ya barsu a nan. Ya zauna cikin kujera yana fidda wani irin wahalallen numfashi yana fesarwa da kyar, yana shaka da kyar. Idan wani ya fada mishi Harrit zata yi mishi haka ba zai taba yarda ba, ya godewa Allah da bai taba kusantar Harrit ba tare da ya yi amfani da kwaroron-roba ba. A take ya fiddo takarda ya dora biro ya rubuta mata sakin aure kamar yadda addininshi ya tanada. Ya leka waje ya kira Raymond da Franklyn ya ce, ya ba su minti goma su fitar da duk wani abu da ke cikin gidan su loda mata shi a waje. Ya leka dakin ya cilla mata takardar sannan ya kara fadi mata da bakinsa cewa ya sake ta saki uku. Ko babu sakin dama auren ya riga ya gurbata a nashi addinin. Ya kuma sanar da su minti goma suka kara yi mishi cikin gida 'yan sanda ne za su raba shi da su. Harrit sai kuka ta ke tana ba shi hakuri, ta kama kafafunshi ta rike tamau! Jan gashinta (blonde) ya baje a bayanta da fuskarta kamar na mahaukaciya. Tuni kwarton nata ya gudu, ta gaban Amiru ya rarrafa ya wuce da rigarsa a hannu, da ya ga ya iso kofa lafiya sai ya taka da gudu iya karfinsa ko motarshi bai dauka ba. Su Raymond ne ke cika umarnin ubangidansu. Masu fushi da fushin wani. Fatali kawai suke da komai dake cikin gidan. Ya fizge kafarshi cike da kyama yana ja da baya tamkar ta dana masa garwashin wuta, a baya in Habibu ya ce kyamar Harrit yake mugun haushinsa yake ji, amma a yau ji yake har zuciyarshi na tashi da kallonta, ya fice babu waiwaye yana mai kara jaddada mata cewa, kada ta sake ya dawo ya ganta ko wani tsinkenta a cikin gidanshi. Bai kara bi ta kan Harrit ba, don ya lura idan ya ce bakin cikinta zai sa a ranshi shi ne zai cutu a banza. Amma alal hakika Harrit ta sanya kasar America ta fice mishi a rai. Dan burbushin kewar kasar da ya rage a baya ya kara zagwanyewa Ya samu kanshi da rashin yarda da kowa, hadi da shi kansa kuwa. Mairo ce kadai yake tunawa ya ji sanyi a zuciyarshi. Itan kam ya yarda da ita da wata irin yarda da bai taba yiwa kowa ba bayan Habibu in ka cire iyayensa, bayan budurcinta data kawo masa cikin girma da daraja, yana da wata irin yarda akanta, yana samun wata irin nutsuwa a duk lokacin da yake tareda ita. Amma ita kanta Mairon a yau sai yaji bazai iya magana da ita ba. Don haka ya kashe dukkan wayoyinshi. Cikin sati daya rak! Duk abin da ya kai shi ya gama shi, hankalinshi ya yo gida kwarai, amma dole ya biya wajen Habibu maganar karatun Mairo. Don haka daga Washington kai tsaye Michigan gidan Habibu ya nufo a Detroit. Habibun ya je da kanshi filin jirgi ya taho da shi. Hakika idan ka dube shi zaka lura cewa, a razane yake, a firgice da al'amarin mata. Ita ma Mairon sai yake ganin kamar kafin ya koma zata yi mishi haka! Don haka ya kulle kanshi a hotel din (RAMADA INN) tare da kulle wayoyinshi don ya samu daidaituwar kwakwalwarshi da tunaninshi. Ba abin da ke tashinshi daga shimfidarshi sai sallah da cin abinci, shi kansa Habibu bai san inda ya shiga ba. Tsayin sati guda sannan ya samu ya yi 'regaining consciousness'. Sannan ya nufo gidan Habibu. Habibun ya ganshi kamar daga sama, koda wasa bai yi gigin fada mishi abin da ya faru ba, don yasan dariya zai yi mishi, dariya har da ta keta, tunda babu yadda bai yi ba ya nuna mishi illar da ke tattare da auren mushrikiya, amma Amirun bai gane hakan ba, sabida giyar soyayya na dibanshi a wancan lokacin, don haka idan yana da kunya ai ba zai neme shi ba. Da ya tambaye shi Harrit sai ya ce da shi, sun rabu ta koma Philppines, bayan idan za a kashe shi bai san inda ta nufa ba. Dina na kicin tana hada musu abincin dare, a yayin da su kuma suke baje a falon suna aikin takardunsu cikin systems. Kallo daya Habibu ya yi mishi ya tabbatar yana cikin wani bacin rai mai zurfi, ya yi tambayar duniyar nan amma zurfin ciki irin na Amiru ya hana shi fadar abin da ke damunsa. Shi kuma Habibun ya takura sai ya ji, daga karshe ya yanke shawarar fada mishi ko da kuwa zai yi mishi dariyar ne, akalla ya samu rangwamen radadin da zuciyarshi ke yi da nauyin da ya danne ta. Habibu ya yi shiru, can kuma ya ce "Ban yi mamaki ba. Shi arne wannan (adultery) a wajenshi ai ba wani abu ba ne extraordinary. Sai a yi hattara, Allah Ya kara tserar da mu daga kutungwila da kaidin ZUCIYA. Amma ni a ganina wannan ba wani abu ba ne da zaka sanya shi a ranka har ya haifar maka da hawan jini, tunda ka san abin da ka aura ai ka aura din. Sannan sabawa mahaifa ai ba abin da ba zai janyo mana ba mu 'yan Adam, don haka sai mu yi fatan Allah Ya kiyaye gaba, Ya sa mu gama da duniya lafiya". Ya ce. "Ina son farantawa Mairo Habibu, kamar yadda ta ke haifar min da nau'o'in farin ciki a kullum. Don haka nake ganin zata dawo nan ta karasa karatunta kamar yadda ta faro shi cikin nasara. Ba zan bari ya kasance ni din na yi silar rabata da burin rayuwarta ba, da tubalin da ka jima kafin ka assasa. Don ko a yanzu na fita na dawo kullum sai na ganta tana bitar littafanta, duk da cewa bata taba yi min korafi akan hakan ba. Ni da na yi mata na ga farin cikinta fiye da kullum, tayi min abinda bata taba yi ba, idan na samu sarari zan dinga lekowa akai-akai insha Allahu". Habibu ya ji dadin wannan karamci da Amiru ya yi mishi, don shi ma abin yana damunshi, don bai san tsarin sa bane shi yasa tun farko bai neme shi da zancen ba. Don haka a washegari suka nufi Michigan State University tare don gyara mata registration dinta. Ya rage saura kwana uku Amiru ya dawo, Hajiya ta yi kiran Mairo, ta hadata da wasu jarkokin magani da zuma roba guda da Mairo ba ta san ko na mene ne ba. Ta ce, ta je ta yi ta kwankwada, ta kawo mata jarkokin kafin kwana uku. Ta bi umarnin Hajiyar don tasan ba zata ba ta abin da zai cuce ta ba, bare wannan magani mai shegen dadi da zaki. A'ah! Ai tun a washegari ta ji yanayin jikinta na sauyawa, ba abin da ta ke bukata sai dawowar Ameeeru, da yake saukar karfe shidda na yamma za su yi, don haka tun safe tana kicin dinta tana hada abincin tarbar angon nata. Da taimakon daya daga cikin masu aikin Hajiya da Hajiyar ta bata don su Sabah duk sun koma makaranta, komai ya hadu. Babu yadda Hajiya ba ta yi ba ta je airport ta tarbo shi ba, amma kunya ta hanata. Wannan na daga cikin halayen yarinyar da suke kara mata kaunarta. Ta lura bayan kunya, tasan mutumcin kanta, kuma ta iya zama da kowa da wata mu'amala ko ya ya ta hadata da shi. Tana sassan Hajiya suna sauraron labaran MBC a lokacin da ya iso, daga bakin kofa ya tsaya, ya tokare kofar da hannunshi na dama yayin da na hagun ke dauke da falmarar din ‘Italian suit’ ruwan toka, wato 'grey' da ke jikinshi. Ya rausayar da kai yana kallonta, da kyawawan idanunshi, ba tare da ita din ta sani ba. Sassanyan kamshin 'miyaki' da ya bakunci hancinta shi ya ankarar da ita tsayuwarshi a bakin kofar n wasu mintuna. Ji ta yi kamar an yi mata gafara sabida farin cikin dawowarsa cikin koshin lafiya. Ta lumshe ido ba tare da tasan lokacin da ta yi hakan ba. Hajiya tana ta magana, amma ba ta ji Mairo ta bata amsa, sun yi nisa a kallon junansu kamar yau suka fara ganin juna. Ta juyo don ta dubi Mairo, a sannan ne ta ankara da inda Mairon ta kafa wa ido. Ta ce "Au, ashe mijinki kika gani kika manta da ni nake ta sambatu ni kadai?". Ya yi dariya ya idasa shigowa dakin. Ita kuwa don kunya sai ta zame ta gudu gidanta ba ta kara lekowa sassan Hajiya ba. Tana shafa a gaban mudubi, ga dukkan alamu daga wanka ta fito. Daure da tawul iya cinyoyinta. Ya bude kofar ya shigo cikin bakaken pyjamas, tana hango shi ta cikin mudubin a lokacin da ya iso gare ta. Ya dora kai a hankali kan kafadunta ta baya, kyawawan fuskokinsu suka bayyana cikin mudubin a jere, a hankali ya sanyata cikin jikinshi ya lullube da hannayenshi, yana shakan sassanyan 'bathrobb' dinta na ‘rasasi’ yana lumshe ido. Ya ce "Tell me how much you misses me, ko ba ki yi kewata ba ne Mairo? Don na ga ke har wata kiba kika kara abunki, ni kuwa ina can tunaninki ya hana ni sukuni". Murmushi kawai ta yi har 'beauty point' din mai kara mata kyau ya lotsa ciki sosai. Ya sumbuci wajen with a very warm kiss, kana a hankali ya soma warware mata tawul din suka soma aikin lada. *** Wata guda da dawowarshi, suka yi shiri suka nufo Kano don yi wa Baffa sallama, kasancewar a cikin satin ne zata koma Michigan. Su Habiba an shiga makarantar ta nutsu don yanzu Mairon da suke wulakantawa ta zame musu uwargijiya da bazarsu suke rawa. (To ina ruwan Allah!) Tuni aka sa Lawan ya gyare musu dakin baki, ya kunna 'burner'. Abinci kam sai wanda suka zaba. Baffa ya ji dadin ganin yanayin da Mairon shi ke ciki, ta cika ta yi bul, ta zama babbar mace, kamar kajin Agric jawur da ita. Ya tarasu duka ita da Amirun ya yi musu kyawawan nasihohi akan rayuwa, da kuma yadda za a yi a ci ribarta. Ya kare da yi masu nasiha akan muhimmancin riko da sallah akan lokacinta. “Ita ce idan ta yi kyau dukkan ayyuka za su kyautata”. Amiru na son Baffan Mairo, sabida sauran mazan jiya ne ba na yau ba, irin wadanda kyale-kyalen duniya ba sa gabansu. Ya cika su da alheri duk gidan, a washegari suka nufo Michigan. Dina ce ta zo ta tarbe su, domin Habibu ya yi balaguro zuwa New-Jersey. Mairo ta rungume 'ya'yanta kamar ta tsaga kirjinta ta sanya su. Suna fada mata, "Mun yi missing dinki Anti Mairo, da gaske ne da Daddy ya ce anyi miki aure da Uncle Amiru???" Inji Bedi. Murmushi ta yi, cikin matsanancin nishadi tana shafa kan yaron, amma ba ta amsa musu tambayar ba. Amirun ne ya ji, ya juyo daga maganar da suke yi da Dina ya bashi amsa cikin daga gira. “yes Muhammad da gaske ne, Daddy is absolutely right! Har ma ta kusa ta kawo wa little Mairo kanwa, nan da wasu watanni kadan”. Da sauri Mairo ta bace a wurin. A ranar Amiru ya juya Washigton don karasa wasu hidimominsa tare da jaddawa Dina amanar rayuwarsa, wato Mairon da ta dusar da hasken sauran matan duniya baki daya daga idanunshi. Sun kulle a daki ita da Dina ana labarin bayan rabo. Dina ta kura mata ido ta ce "Anya Mairo? Jikin nan naki babu bayani? Irin wannan fari da kyau haka sai ka ce mai shafe-shafe? Ko dai kwanan nan za fara goyo ne? Naji Amiru na fadawa yara dazu na dauka wasa yake" Mairo ta rufe fuska da tafukan hannunta, ta ce "Kai Anti Dina, wallahi ba ni da komi. Karewa ma yanzu haka period nakeyi. Ni fa tunda na je gidan dakina daban nashi daban. Kuma ba sai ana kwana daki daya ne ake yin cikin ba?". Dina ta kyalkyale da dariya ta ce. "Amirun? To abar kazar cikin gashinta tunda ba kya son a fige ta kada in zama babbar banza". Ta jawo lokarta ta soma fiddo mata magungunan mata masu kyau da tsada 'yan Indonesia data ke saya tana yi mata bayanin tsarin shan su. Mairo ta ce "Maganin mene ne?" Dina ta murmusa, ta ce, "Maganin basir ne, ke dai ki dinga sha don da alama akwai basir a jikinki tunda ga shi nan duk kin yi fari". Mairo ta yi dariya. Ta rasa dalilin da yasa kullum Dina ke treating dinta yarinya kamar Little Mairo. Idan dai wadannan magangunan ne ai tunda ta zo gidan ta ke ganin Dinan na shansu, sai dai ba ta taba tambayarta ko na mene ne ba. Amma yanzu ai ta yi girma da hankalin da zata san amfaninsu. Daga baya ko me Dinan ta tuna? Ta zaro ido ta ce "Ke! Bani magungunan nan bai kamata ki fara amfani da su ba, sai mun je asibiti anyi checking dinki don ban yarda da ke ba. Mai juna biyu ba ta amfani da irinsu". Mairo ta bata fuska kamar ta yi kuka, don gani ta ke kamar Dinan na kallon abin da ta ke yi a goshinta. Ta tashi gudu tayi dakinta. Dina sai ta yi dariya, kuruciyar Mairo da halayenta na alkunya suna burge ta matuka. Satin Amiru daya da tafiya sai ga shi kamar an jefo shi. Tana kicin tana hadin salad don haka Dina ce kadai a falo, ita ma ba ta jima da dawowa aiki ba, ta sanya Mairon ta hada mata salad zata ci. Kararrawar kofar shigowa ta yi kara, ta umarci Lynder ta bude. Amiru ya bayyana a falon cikin bakaken suit-spanish. Ta daga kai tana kallonshi tare da amsa mishi sallama, ganinshi wani 'as a smart pace' (afujajan) ya bala'in ba ta dariya. A gajiye ya zauna cikin kujera idanunshi a kwance ya ce "Dariyar me kike yi min?" Ta ce "Ganinka na yi kamar an jefoka, lafiya dai ko?" Ya ce "Da babu lafiyar ai ba za ki ganni ba, sai dai sako. Ina kanwar takin nan ne? Yanzu haka kina nan kina hadata da wadannan girke-girken naki na tsiya". Ta ce "Au na tsiya ne, amma idan an baka kake ci?" Bai amsa mata ba ya nufi kicin inda ya jiyo motsin tangaraye. Ta juya baya ta takarkare tana bude gwangwanin 'heinz-beans' ya mika dogayen hannuwanshi ya rungume ta. Ya soma sauke ajiyar zuciya mai nauyi. Kwanaki bakwan nan da ya yi ba tare da ita ba, jinsu ya yi kamar shekaru bakwai. Ka zalika ita ma Mairon, don dai ta kasance mai zurfin ciki da kawaici ne. Amma ta yi missing din mijinta yadda harshe ba zai iya bayyanawa ba. Sun yi nisa cikin duniyar faranta ran junansu, kafin Mairo ta ankara da inda suke, ta yi kokarin kwatar kanta. Ya dago habarta da hannun damanshi yana son kallon kwayar idanunta, amma bai yi nasarar hakan ba sabida matsananciyar kunyarshi da ta lullube ta. Ta yi azamar hankade shi sabida warin 'aspen' da ta tsinkaya cikin bakinshi. Ya sake kamota ta fuzge, ya ce, "Haba Mairo? Mairon Dina, Mairon Yaya Habibu?" Zata fice ya sha gabanta a galabaice, ya ce, "Kina so Mala'ikun rahma su soma tsine miki ko, bayan da kina ta kwasar lada?" Inda abin da Mairo ta tsana to wannan furucin ne, kamar ta yi kuka ta ce, "Ni na ce ka sha taba? Tun a gida ka ce min ka daina sha, amma ai ga shi nan na ji-ta a bakinka". Ya rufe mata baki, ya ce, "Wallahi bazan kuma ba. Wannan din ma a jirgi aka ba ni. Ba kudina na sanya na siya ba. Ce miki nayi “bazan kuma sayen taba ba”, ba “bazan kuma shan taba ba..” Sun ba ni 'wine' ne, ni kuma na ga da na shata ai gara na sha tabar". Ta zumbura baki, tana toshe hanci ta ce. "Ni don Allah ka ba ni hanya na wuce..." Amma fa banda kaduwa ba abinda jikinta ke yi, Amiru ya bala'in sanin 'weakness' dinta. Karfin halinta da jarumtakarta suna ba shi mamaki. Kiri-kiri ga shi tana cikin kewar mijinta, a idanunta da gangar jikinta, amma a fatar baki ta nuna ba haka ba ne. “Ko in baki (hanky) ki toshe hancin da kyau??” Kanshi ya tura cikin gashin kanta ta baya, bayan ya cillar da 'bound' din da ta daure gashin da shi. Yana shakar kamshin kumfar 'pert-plus' da ta ke amfani da shi ba tare da ta sa wa gashinta 'relaxer' ba. Amma sai ka rantse kullum 'relaxer' ta ke shafa mishi. Can cikin kunnenta yake rada mata. "Rakiya za ki yi min Mairo". Da sauri ta ce "Zuwa wajen budurwarka?" Ya yi dariya, ya ce. "Ga budurwata nan ina tare da ita, shopping zan yi". Ta ce "Ni ba zan bika ba kullum kana yawo da wadannan gardawan masu shegen kallon tsiya kamar wasu 'body-guard' dinka". (Raymond da Franklyn). Yayi dariya. Ya ce "To zan sallame su. Mu biyu zamu yi tafiyarmu, sannan ba shan Aspen a hanya, in kin ganni zan saya ki kwace credit card din, hakan ya yi miki?" Ta gyada kai cikin gamsuwa. "Amma kai zaka fadawa Anti Dina". "Idan don wannan ne, ta kwana gidan sauki, uuwata ce ita ko kanwar ubana? Daga kawo ajiya?” Abin ya bata dariya amma ta gimtse. "To bari na karasa hada mata salad din, yunwa take ji". Har zuwa lokacin bai sake ta ba, ya bi ya kankane ko'ina na jikinta. Sai faman sunsunarta yake yi kamar zai hadiyeta. Sai da ta hada da magiya sannan ya sassauta rikon da ya yi mata. Tare suka fito ta isa ga Dina ta mika mata farantin, ta nufi dakinsu don ta kimtsa. Wanka ta sake ta zuba riga da siket na wani material yellow mai santsi, ta nada dan bakin mayafi a kanta, ta matse da fil ta kara feshe jikinta da turaren (fahrenheit). Tana kokarin saka takalmi ta jiyo Dina na kwala mata kira, don haka ta dauki jakarta 'polo' mahadin takalmin da ke kafarta ta fito. Ba ta san me ya fadawa Dina ba, ta ce "Amiru ya ce za ki raka shi shopping ko? To sai kun dawo". Suka hada ido ya daga mata gira, ya kashe ta da murmushi. Ta yi hanzarin sunkuyar da kanta. Ya mike yana kiran Raymond ya fada mishi su je sai ya neme su, yana tare da Madam dinshi. Ya karbi makullan motar Mairon hannun Dina, suka fito. Tafiya suke sannu a hankali, irin tafiyar da ke sanya nishadi a zuciyar ma'aurata, kuma irin tafiyar da ke kara wa masoya kusanci da juna. Babu wanda ke cewa uffan sai zuciyoyi kadai suke magaba. Ya mika hannu yana karo sautin Abdurrahman Sudaith da ke tashi a hankali cikin radiyon motar, cikin suratul Anfal. Hankalin Mairo na kara nutsuwa da mijinta, wanda dan zaman da suka yi na tsayin watanni ya sanya ta ke fuskantar kyawawan halayensa a hankali. Wadanda ada bata yi tsammani ba. In tayi la’akari da irin tsarin rayuwarsa da bigiren da yake rayuwa a ciki, da kuma irin mutanen da yake hulda da su. Ko su Raymond sun isa su dulmiyar dashi cikin dabi’un nasara. Sai ta tadda akasi ga tunaninta. Da farko dai ta fahimci Amirun ba’a kada shi a magana, ko me ka gaya masa zai baka amsa daidai da maganarka, ko ya baka wadda ta fita daraja, kuma ba shi da munafunci, kai tsaye yake fadin abin da ke cikin zuciyarshi ba tare da la'akari da cewa, zai yi wa mai sauraronsa dadi ba ko a'ah? Sannan Amiru mutum ne mai kula da sallah, da ba ta dukkan hakkokinta. Har ga tabon sujjada nan rangadede a kan goshinsa. Ga son 'yan uwansa da iyayensa da kulawa da su, irin mazan da duk son da suke wa mace ba sa hada shi da na iyayensu. Yana da ban dariya, yana da barkwanci, sai dai idan miskilancin ya motsa ya fi mahaukaci ban haushi da takaici. Ba ta kai ga gama tunaninta ba ta ji yana zungurin kugunta da mukullin mota. Ta juyo a hankali tana kallonsa, soyayyarshi na kara kamari a tare da ita. Kamar yasan me ta ke tunanin, ya kamo hannunta ya rike cikin nasa, ya kwantar da kai a kafadunta, ya dora mata dukkan nauyin jikinshi... "Mairo kada ki bar ni. Ba ni da harshen da zan fada miki adadin soyayyarki da ke cikin zuciyata. Ban taba son wani abu a rayuwata kwatankwacin yadda nake sonki ba, idan kika dauke iyayena. Ban taba yin soyayya ba Mairo sai a kanki. Nasan kin aure ni ne ba bisa son ranki ba, amma......" Ta yi hanzarin kai yatsunta ta toshe mishi baki. Ta kankame shi sosai jikinta yana rawa. "Kayi min alfarma kada ka kara yi min wannan zargin, domin kuwa Allah shaidata ne akan cewa na aureka ne da zuciya daya, cikin amincewa kaina cewa, kai ne mijin da Allah Ya zaba min; kai ne zabin Allah a gare ni. Daga lokacin da na fara ganinka, na ji wasu abubuwa sosai a zuciyata. Duk da soyayyar Uncle dina da nake fama da ita a wancan lokacin hakan bai hanani ba ka wani muhimmin gurbi a zuciyata ba, gurbi na ‘auratayya’ ba soyayya ba. Na kalubalanci tunanina ne a lokacin da cewa yaudara ce. A hankali na gane hakan ma ba ya zuwa sai da soyayya! Soyayya ta da Uncle Junaid wani abu ne da ya shude a wata rayuwata ta can a baya..., Past is past Ameeru, and you are my present...!!!" Amiru ya wani irin kankame Mairo yana mata sumba mai tsayi da zurfi, tsayin wani lokaci mai tsawo, kamin su samu nutsuwa cikin zuciyoyinsu. A yau ya samu wani irin kwanciyar hankali irin wanda bai taba samu ba tun haduwarsa da Mairo. Tada motar yayi suka harba kan titi. Ba su tsaya ba sai a shagunan da ke karkashin 'Sommerset mall'. 8/6/21, 1:16 PM - Kawata: 55555555555 Shi kadai ya shiga ya yo musu duk sayayyar da zai yi. Ta duk abinda zasu bukata na kwana uku. Ya bar Mairo cikin motar. Tsabar kishi irin na Ameer bai yarda da shiga da Mairoßs irin wadannan wuraren ba, bai tsaya a ko'ina ba sai a otel din 'Hyatt Regency' inda Amirun ya yi masauki. Hotel ne na manya, na daga wane sai wane. Ta dube shi a razane, a sanda ya kashe motar, sanda ta fahimci cewa a otel suke. Kamar ta yi kuka ta ce. "Haba don Allah? Me zan ce da Anti Dina?" Ya langwabar da kai abin tausayi a masangalin kujerarsa, tsayin lokaci bai ce mata komai ba, a cikin lumsassun idanunshi kadai ta gama samun amsar duk wani uzurin sa da dalilinsa, da kyar ya ce. "Ba kya tausayina ko Mairo? For quite a week kenan ina suffering. Sabida ke nazo, tun daga Nigeria har Michigan. Sannan idan na tafi na barki zan jima ban zo ba, sai kun yi hutun karshen semester, ban sanki da halin rashin tausayi ba. kada ki fara ta kaina…...!!!” Kalaman sa sun gama kashe duk wani kuzarinta. Kwayar idanunsa sun gama kassarata. Ba yadda ta iya, dole ta zuro kafafunta ta fito. Zuciyarta na gaya mata ko akan titi Ameeru yakeso su rayu yau zata kasance tare dashi, gata dama da rarraunar zuciya, wadda ta afu ga son Ameerun with infatuation. A kwanaki ukun da suka yi cikin otel din 'Hyatt Regency' tamkar wani sabon babin amarci ne Amiru da Mairo suka balle. Mairo ta ga soyayya a gun Ameeru irin wadda a duk karance-karancen Novels dinta, ba ta taba katari da irinta ba, domin Amiru karshe ne, a fannin nuna soyayyah. A yau zai maida ita gida, domin jirgin karfe hudu na yamma zai bi zuwa gida Najeriya. Tunanin Mairo na yadda za ta fuskanci Dina ne da Yaya Habibu idan ya dawo ya ji ta bi miji, kwana da kwanaki ba a gansu ba. Har kuka ta yi saboda damuwa, don ta lura shi ko a kwalar rigarshi. Ba karamin tausayi da dariya Mairon ta ba shi ba. Don haka ya shiga lallashinta, yana nuna mata wannan ba wani abu ne na tada hankali ba. "Shi Yaya Habibu da Dinar ba daki daya suke kwana a gabanki ba? Su ba su ji kunyarki ba, sai ke ce mai jin kunyarsu akan haka?" Ta balla mishi harara cikin hawaye. Ya tarairayota ya rungume yana dariya, ya ce. "Shikenan ki barni da su, ni zan fitar da ke". **** Lokacin da suka iso gidan Habibu da Dinan ne suke 'lunch' tare da su Muhammad. Cikin bagararwa Yaya Habibu ya saci kallon Mairon da ke bin bango tana son ta shige dakinta, ya ce. "Ai na dauka kun wuce gida Najeriya ne?" Amiru ya yi dan murmushi, sannan ya ce. "Idan mun wuce ina ruwanka? Ni bana son aikin sa ido wallahi". Dina ta yi murmushi tana jinsu suna ta yi, Amirun na cewa. "Sa ido sana'ar banza, Yayan banza, Yayan kwabo". Habibu ya dube shi, ya ce. "Na ji dai, tunda ni dai mace ba ta taba kwantar da ni a gadon asibiti ba". To a nan ya kashe bakinsa, don bai kuma tankawa ba. *** C ike da himma Mairo ta dasa karatunta daga sabuwar shekara, duk da su Ir'eesh sun wuceta, ya kasance ta koma farkon shekara ta biyu. Habibu ya ba ta wayarta, bayan wadanda Amirun ya mallaka mata guda biyu irin wadanda ba ta taba gani ba. Don haka duk dare suna makale a waya suna fadawa juna how much they miss each other. Yadda ba ta iya sakewa su yi hira fuska da fuska, a waya idan ka ji su, sai ka sha mamaki. Kullum tambayarshi shi ne, har yau babu ajiyarshi ne? Da ya fadi hakan zata yi sauri ta kashe wayar, sabida kunya. To haka rayuwarsu ke tafiya, cikin so da kauna, ba sa taba gundurar juna. A Najeriya ne ko a Michigan, har Mairo ta kare karatunta, ta fiddo kwalin first class degree a B.Sc Sociology. Har zuwa wannan lokacin shiru, babu haihuwa babu alamarta, don ko batan wata Mairo ba ta taba yi ba. Tun abun na damunsu har suka hakura suka fauwalawa Allah. Sai dai kuma kamar yadda kowanne dan Adam ba ya rasa makiya, to hakan ce ta faru da Mairo daga dangin Amiru, musamman a Gaya da suka fara kishin-kishin Amiru ya auro musu juya, don ma Hajiya tana tsawatarwa ne amma har su Sabah sun soma sauya mata fuska. Aka soma yi wa Amirun tushen 'yammata, 'ya'yan gata, kyawawa wadanda suke ganin zasu iya gogawa da Mairon da duk abin da ta ke takama. Zuwa lokacin shi ma Habibu ya yi 'retire' daga 'barclays', haka Dina ta bar kotun da ta ke aiki. Sun tattaro da 'ya'yansu duka sun dawo gida Najeriya garin Abuja, cikin unguwar colorado close. Don haka Mairo cikin farin ciki ta ke, ga ta ga iyayenta, wadanda su ne kadai ta ke gani ta ji dadi, kasancewar Hajiyar ma ta soma daukar hudubar 'ya'yanta da 'yan uwan mijinta na Amiru ya kara aure. Daddy bai san abin da ke faruwa ba na matsalolin da Mairo ta soma fuskanta cikin gidan ba. A lokacin tana hidimar kasa a nan jami'ar Abuja, ta kai ga ko ta gaida Hajiya a ciki ta ke amsawa don gani ta ke Mairon ta mallake mata da, yadda har ba ya damuwa da samun dan kansa. (Matsalarmu ke nan al'ummar Hausa, babu ta yadda za a yi a ga mace na zaune lafiya da mijinta yana sonta, yana gudun bacin ranta, sai a ce ta mallake shi. An fi so a ji kullum yana kawo kararta ana yi musu sasancin sulhu, ko ya dinga aura yana saki, ko ya dinga aibatata cikin yan uwansa, Allah Ya sa mu gane mu gyara zuciyoyinmu, amin). A yau ne Amiru ya shirya musu 'wedding anniversary' na cikarsu shekaru biyar da aure. Taro ne da ya tara manya-manyan ma'aikatan bankunan Najeriya, bankunan kasar America, irin su World Bank, Barclays, Bank of America, Comerica, Citigroup, HSBC, Chase... da sauransu. Abokansu na karatu ne da yawa da suka watsu a wadannan bankuna suka gaggayyato. Taron wanda aka gabatar da shi a wani conference hall na 'hotel' din 'Nicon Noga' ya yi matukar yin armashi, kowane bako da maidakinsa, wato by couple'. Mairo da Amiru sun samu kyaututtuka na ban mamaki daga 'yan uwa da abokan arzikinsu. Kudi wannan tsurarsu da Mairo ta samu sun tasarwa lissafi mai girma, ba’a maganar sauran kadarori irinsu gidaje, hannun jari da sauransu. Daddy kadai abin da ya bayar ya girgiza kowa, wai! Ina wuta a jefa marainiyar Allah Mairo a wajen kannen Amiru, dangin Hajiya da dangin Daddy da suka zo daga Gaya. Sun sha alwashin idan Habibu a tafe yake yana tsaface musu Da ta yadda har ba ya jin shawarar kowa sai tashi, baya ganin owa nasa da gashi sai shi, to su a can suka kwan, kuma acan suka wuni. Gadararsu shi ne Amiru shi ne silar arzikinshi, wannan bai ishe shi ba, sai da ya kakaba mishi kanwarshi da a yanzu ta zame musu alakakai, karfen kafa. Don haka sun sha alwashin sai Amiru ya yi auran dangi, kuma sai sun raba shi da Habibun koda za su yi yawo tsirara ne. A wannan dan tsukin Mairo ba ta samun zama, sabida shirye-shiryen fara karatunta a 'Wayne State University' da ke Michigan. Komawa karatun da ya janyo mata kace-nace da dama har ta gwammace dama ba ta tarki zancen ba. Domin Hajiya ta kira Amiru kai tsaye ta fada mishi cewa ba ta yarda ba. Idan ba zata yi karatun a nan ba, to ta bar shi, amma sun daina daukar wannan rainin hankalin na Habibu da mace tana gidan aure zata tsallake ta tafi wata uwa duniya wai karatu. Amiru ya sha mamaki kwarai, don bai taba ganin ranar da wani sabani ya gitta tsakanin Hajiya da Mairo ba. Biyayya ta ke mata tamkar ta yi mata sujjada. Hajiyar da ke fada da shi idan ya batawa Mairo rai, amma yau ita ce ta ke mishi magana kamar ba ta taba sanin Mairon ba. Bai san ba abin da 'zuga' da 'karfar baka' ba sa jawowa ba. Cikin nutsuwa ya soma yi mata bayani cewa. "Hajiya babu hannun Habibu a cikin wannan lamari. Idan ma da wanda yake da ruwa a ciki to ni ne. Don ni na amince mata, Mairo tana karatunta na aure ta, wanda hakan har ya janyo mata asarar shekara guda, kuma Hajiya wanda ya saba karatu a waje ba zai iya karatu cikin gurbatattun jami'o'inmu ba. Da wannan dalilin da kuma wasu da yawa ya sa….." "Kai! Rufe min baki!! Shirmen banza shirmen wofi, sallamamme , bawan mace. Da dai ba a san asalin balbelar ba ne zata zo ta ce da mu daga Makkah ta zo, kuma kowa ya samu rana ai sai ya yi shanya inda yake so. Don haka ka tashi ka ba ni waje, maganar karatu na soketa. 'Ya'yan Abdurrahman Gaya ma a nan suke karatun, bare wata 'yar karkarar da ko kwalta babu. Allah dai Ya isa tsakanina da Habibu, tunda ya mayar min da da sammatacce. Ya kanainaye dukiyarka, kanwarshi ta kanainaye zuciyarka ta tsiyata ka, don ba na jin abin da ta samu din nan kai ka samu rabin-rabinsa. Sabida haka wannan hadin gwiwar da aka yi aka bude Habib Bank raba shi za a yi, wallahi ba zan yarda ba. Ku biyu ke da banki, amma sunasa ne shikadai keda bankin. Sabida kai wawa ne. Don haka na ba ka kwanaki bakwai ka kawo min takardun komi mai nuna ka raba dukiyarka da ta Habibu, idan ba haka ba, wallahi TSINE MAKA ZAN YI!!!" Haka ya taso ya fito ko gabanshi ba ya gani. ya yi taga-taga zai fadi, ya yi saurin dafa bango. Kanshi ya kulle tamau, kwakwalwarshi ta daina aiki. Bai san yaushe Hajiya ta koma haka ba, bai san laifin da Habibu da Mairo suka yi mata haka da zafi ba. Bai san me zai cewa Habibu ba. Ya yi tunanin ko ya samu Daddy ya fada mishi ya ba ta hakuri, kuma ya yi tunanin kada haka ya janyo ya kara laifi a wajenta. Don haka a kwanakin da suka biyo baya duka Mairo ta kasa gane kan Amirun nata. Kullum yana kwance a daki yana tunanin ta inda zai bullowa al'amarin ba tare da ya batawa kowannensu ba. Don ta Mairo mai sauki ce, yasan ba ta musu da shi, idan ya ce bai yarda ta koma Michigan ba yasan ba zata nuna bacin rai ba, zata bi umarninshi. Amma Habibu fa, me zai ce mishi? Mutumin da ke dawainiya da dukiyarshi dare da rana tana kara bunkasa tana kara habaka shi yana kwance a gida, sai ya ga dama ne zai dan tabuka wani abu. Ba ya son sunan Hajiya ya fito ko kadan cikin lamarin kada mutuncinta ya zube a idanun Habibun. To wannan tunanin su ne suka hadu suka haifar mishi da ciwon kai mai tsanani, wanda ya kai shi har tsayin kwanaki biyar da yin maganarsu da Hajiya amma ya kasa yin wani yunkuri. Ga shi yau saura kwana biyu kwanakin da ta deba mishi su kare. Mairo ta shigo cikin shirin barci dauke da dan karamin faranti a hannunta. Ta zauna a gefen gadon ta dauko kanshi ta dora a cinyoyinta, bayan ta ajiye farantin da ke hannunta bisa durowar jikin gadonsu. Ta daura kanta akan nashi tana jin yadda ya yi zafi rau. Cike da tausayawa ta ce. "Don Allah A.A (kamar yadda ta ke kiransa idan ta so nishadi, wato Amiru Abdurrahman) ka daure mu je asibiti tunda ka ki yarda na kira Dr. Fred, ya kake so na yi? Jin ciwon kan nan nake kamar a cikin jikina, sannan ka ce ba zaka hadiyi magani ba? So kake nima ciwon ya kamani sabida damuwa?" Sai ta sa kuka sosai, ta tura kai cikin kirjinshi. Ya mika hannu yana shafar gadon bayanta a hankali. Amma bai ce komi ba. Shi kadai yasan halin da zuciyarshi ke ciki. Kukanta na tsuma mishi zuciya, yana kara gigita shi. "Ya isa Mairo, ya isa don Allah, ba ni maganin na ji zan sha". Ta dago da idanunta jage-jage da hawaye tana kallonshi, kwanaki biyar kacal, duk ya rafke, ya rame, ga wata kasumba mara tsari ta fara bayyana, kamar ba Amiru mugun dan kwsalisar nan ba. Ta mike zuwa lokar jikin mudubi, ta dauko kwayoyin paracetamol ta ciri biyu ta hada da gorar ruwan 'swan' mara sanyi ta ba shi. Da kyar ya ke hadiya yana bata fuska don shi sau dubu gara a yi mishi allura goma da dai ya hadiyi kwayar magani. Ya tura yatsunshi cikin sumar kanshi yana cudawa a hankali. Mairo ta gane kwarai, akwai muhimmin abin da ke damun Amirun nata. Wanda zurfin cikinshi ba zai bari ya bayyana ba. Sai ita ma ba ta takura da lallai sai ta ji ba. Yinin yau ma ya kare baki daya ba tare da ya hassala komi ba. Ya rage gobe ne wa'adin da Hajiya ta dibar mishi zai cika, suna kwance kankame da juna kamar masu jin tsoron kada wani abu ya gitta a tsakaninsu. Ya yi gyaran murya ya ce, "Maryam". (Sunan da bai taba kiranta da shi ba). Ba ta amsa mishi ba, illa ta kalli kwayar idanunshi ta cikin dan hasken fitilar barci (dim light). Ya sake kiranta a karo na biyu, ya ce. "Alfarmarki nake nema Mairo, za ki yi mini?" Ta ce "Babu alfarma tsakanina da kai, sai biyayya da bin umarni. Don haka fadi abin da kake so, ni kuma ji da bi shi ne nawa". Ya kara lullube ta da katafaren kirjinshi, ya sarke 'yan yatsunsu cikin na juna, ya ce. "Maganar komawarki karatu Michigan, na ke so ki bari, ki yi hakuri, ki yi a nan Gwagwalada ya fiye min kwanciyar hankali". Ta ce "Idan don wannan ne ai babu komai. Sai dai na fi son na yi karatu a jami'a mai nagarta da tsohon tarihi, kamar Ahmadu Bello ko jami'ar Bayero". "Duka ki hakura, ki barsu, tunda kika ji na ce 'alfarma' to alfarmar nake nema da gaske. Kin san haka kawai bazan sa ki yin abin da ranki bai so ba, don haka ki yi min uzuri". "Na yi maka A.A, Allah Ya ba ka lafiya". *** A yau ne Hajiya ta yi kiranshi don jin inda suka kwana. Ta tsare shi da dara-daran idanunta, kafarta daya akan daya cikin luntsumemiyar kujerar falonta. Ta ce. "To yaya, kai nake saurare?" Ya ce, "Maganar tafiya karatu ai an barta Hajiya, tunda ba kya so". Ta mika mishi hannu, ta ce. "To ba ni takardun". Ya yi wuki-wuki da ido, can ya ce. "Habibun ne ba ya nan, idan ya dawo za mu zauna a ware a kawo miki……..". Sai hawaye sharr-sharr wasu na korar wasu, domin gani yake Hajiya ta gama tozarta shi, a duk ranar da ya doshi Habibun da wannan zancen. Domin Habibun zai yi zargin abubuwa da dama, ciki kuwa har da tunanin ko Amirun na zarginshi da cin amana ne, ba zai taba kawowa ranshi Hajiya ce ta sa shi ba sabida yadda ta dauke shi kamar dan cikinta, shi ma yake daraajjata kamar mahaifiyarsa. Hajiya ta kama baki, tana cewa. "Yanzu sabida ina so na rabaka da abin da zai cuce ka, shi ne za ka sanya ni a gaba kana yi min kuka?" Ya dago sosai yana dubanta da idanunshi da suka kada suka yi jawur. Muryarshi abin tausayi ya ce. "Hajiya, Habibun ne zai cuce ni?" Ta girgiza kai. "A'ah, ba zai cuce ka ba. Ni uwarka ni ce zan cuce ka. Habibu sai ya je kauye ya biya malamansa. Tashi ka je, na yafewa Habibu da kanwarshi Mairo kai, idan har ba zaka kawo min takardun komi na dukiyarka ba. Kuma zan maka Habibu a kotu sai ya ba ni dukiyar da na!" Zuciyarshi ta bushe da etsoro da al'ajabi. Ya ce, "Hajiya me ya yi zafi da za ki kai Habibu kotu? Ki kara min alfarmar kwana biyu. Na yi alkawarin zan cika umarninki ko da hakan shi ne aiki na karshe da zan gabatar a rayuwata". Fitowa ya yi zuciyarshi na suya, ya zaburi mota bai tsaya a ko'ina ba sai a kofar gidan Habibu. A lokacin Habibu na shirin shiga mota zai fita, shi kuma yana danno hancin motarsa (Camero, 2 door) cikin 'gate' din Habibun. Don haka ya fasa shiga motar ya jirashi har ya karaso ya fito daga motar.ŕ Ba karamin faduwar gaba ce ta samu Habibun ba ganin irin halin da aminin nashi ke ciki. Suka rankaya suka koma cikin gidan. Dina ba ta nan, ta je Malaysia ita da yara, duba jikin mahaifinta da ba shi da lafiya. Habibu ya isa ga firij, ya dauko mishi gwangwanin 'coke' ya bincire hancin ya mika mishi ba tare da sun gaisa ba. Ya karba ya yi kurba daya, amma ya kasa wucewa a makoshinsa. Dole ya furzar da na bakinshi idanunshi sun kara kadawa sun hargitse. Habibu ya zauna a gefenshi, ya ce "Be a man, plz! idan kana raye ba abin da ba zaka gani ba". Ya rausayar da kai cikin amincewa da kalaman Habibun. Ya ce "Alfarmarka nake nema, sai dai bana son ka tambaye ni dalilina, na yin hakan". "Ba zan tambaye ka ba Amiru. Fada min komi tsaurinta". "So nake na janye komi nawa daga cikin 'Habib Bank!!". Habibu ya yi shiru, domin Amiru ke da kaso 60% wanda hakan ke nufin durkushewar bankin da ya faro da nasara cikin shekaru biyu kacal da kafuwarshi, wanda ke nufin shi kadai (Habibun) ba zai iya 'running' bankin ba. Ya tabbatar makiya sun shigo cikin al'amarinsu, amma bai ga laèèifin Amirun ba, wanda da gani kasan tursasa zuciyarshi yakeyi, wajen furta kalaminshi. Ya ce "Idan don wannan ne, ai babu damuwa Amiru. Idan har hakan zai samar maka kwanciyar hankali, ka ba ni kwana goma, insha Allahu komai naka zai dawo hannunka. Sai dai ina so ka samu lauya, wani daban, ba Dina lauyar bankinmu ba". Ya ce "Ni ba ni da wani lauya". Habibu ya ce "Dole sai ka nemo". Ya juyar da kai yana kwararar da hawaye, ya ce "Daga yau ba zan kara neman kudi ba, tunda su din fitina ne. Ta yadda har wasu suke ganin su din (kudi) sun fi mutumci da amana, Ya Allah Ka tsiyata ni……….." A gaggauce Habibu ya toshe masa baki. "Kana hauka ne? Kada 'frustration' (bacin rai) ya sanyaka fita daga imaninka. Ka je ka samo lauya, mu yi abin da zai kwantar maka da hankali". "Ni na ce da kai hakan kwanciyar hankalina ne?" "Ba ka ce ba, don haka abar kazar cikin gashinta ba sai an fiffigeta ba". Cikin satin Habibu, tare da taimakon Barrister Dalha wani abokin aikin Dina daya daga cikin lauyoyin 'CBN' da Barrister Mujahid lauyan 'starling' sun hattama komi na dukiyar Amiru, ta koma hannunshi da sunanshi da sanya hannunshi. Ya kwashi takardu cikin 'briefcase' ya yi sallama a dakin Hajiya. Kallo daya ta yi mishi ta ga yadda ya zabge, ya yi zuru-zuru sai karan hancin da idandanun kadai, amma hakan bai sa ko kadan zuciyarta ta russuna ba, da dai ta kyale Habibu da kanwarshi su yi galaba a kanta. Tunda sanda ta ke nakudar abinta bayan rainonshi cikin mahaifarta, har wata tara da dawainiyarshi zuwa girmanshi, ai ba su zo sun tayata ba. Don haka ta kudure sun daina cin arzikin Amiru, kowa ya ci gashin kansa. Ya zauna a kujerar da ke fuskantarta, kwakwalwarshi na juyawa. Ya mika mata 'briefcase' ba tare da ya iya hada ido da ita ba. Ta bude ta zaro takardun ciki ta sanya 'medicated glass' dinta tana dubawa daya bayan daya. Ita kanta ta razana da ganin abin da Amirun ya mallaka a 'yan kananan shekarunshi. Bayan ta gamsu da ingancinsu, ta maida su inda suke tana murmushi, ta ce. "To ko kai fa? Ba ga shi ba yanzu sai yasan zafin nema ba ya tashi daga cima-zaune? Yanzu wane kasuwanci zaka soma da wadannan din?" Ya kalle ta kawai bai yi magana ba. Ta dauka bai ji ba ne, don haka ta sake maimaitawa. Ya ce ba tareda ya dubeta ba, "Sadakar da su zan yi". "Au fushi ka yi, sabida ina yi maka gata Amiru?" Ya ce "Ya ya za a yi na yi fushi da ke Hajiya? Ina juya su, kin ce in kawo miki. Na kawo miki kuma ki ce me zan yi da su? Ban iya wani kasuwanci ba, bayan wanda nakeyi, ni ma'aikaci ne. Aikin banki shi ne wanda na iya tsawon shekaru goma. A yau kin ce na barshi, don kada Habibu ya samu dan wani abu a jikina, wanda bai taka kara ya karya ba. Bayan kin san duniyar cudarni in cudeka ce, kuma shi ma ba matsiyaci ba ne, yana da rufin asirinshi wanda da kadan ne bai kai nawa ba. Haba Hajiya! Shekarata nawa da Habibu bai cuce nin ba sai yanzu da muka zama daya?" Hajiya ta ce "Rabi (half) kuka zama ba daya ba, sallamamme, bawan mace. Tunda ba ka so ka yi zuciya har kana cewa sadakarwa zaka yi, ni ina so, zan yi maka sadakar, amma ba duk ba. Ranar da tsiya ta isheka ka waiwaye su, nima ina da 'account' din da zan adana maka su su hayayyafa ba Habibu ne kadai ya iya juya sisi ya koma kwabo ba". Duk abin nan da ake Daddy bai sani ba, don shi ba mazauni ba ne, sannan ko da wasa Hajiya ba ta yi gigin sanar da shi abin da ta yi ba, don tasan bazai goyi bayanta ba. Sai su Khalisa da Nina wadda ke aure a Lagos sune 'yan abi yarima a sha kida, duk suka yi ta tsalle. Nina ta ce "Mun gama da wannan, saura 'yar kauyen Gurin-Gawa, don Allah Hajiyarmu ki yi mana waje-road da ita". Hajiya ta ce "Ku barni da su, duk na ishe su, ko ba ta yi waje ba, ai ta yi zaman boranci idan na aura mishi wadda zata cika min gida da 'ya'ya". *****÷ 8/6/21, 5:15 PM - Kawata: F An debi watanni biyu kwarara, Hajiya na tarairayar danta don dai ta wanke dattin ta dake idanunshi, tana kuma nuna kulawarta akan Mairo, wadda ita kuma ba ta san tana yi ba, karatunta kawai ta sa a gaba. An yi bikin su Sabah tun shekarar da ta gabata, bayan sun kare karatunsu. Don haka yanzu sassan Hajiya babu kowa, daga ita sai 'yan aiki. Watakila hakan ne ya sa ta kwallafa ranta ga son ganin 'ya'yan Amirun, tunda sauran jikokinta iyayensu maza ba za su ba ta ba. Yau da ya shigo gaishe ta da safe, cikin sakin fuska ta amsa. Bayan sun gaisa ta janyo wata dirkekiyar jarka irin wadda ake zuwa da zam-zam daga Saudiyyah din nan, cike ta ke taf da ruwan rubutu bakikirin da shi ta girgiza ta tsiyayo a kofi ta mika mishi. "Ungo shanye ka ba ni kofin". Ya ce "Na mene ne Hajiya?" "Maganin sammu da tsarin jiki ne, ko ba zaka sha ba? Idan ka shanye shi duk wani makaru da ke jikinka zai karye, don haka shanye ka ba ni kofin". Bai yi musu ba ya karba ya soma sha a kyankyame, don kam shi Amiru tun fil'azal mutum ne mai kyankyami matuka, ko (spring water) ba kowanne ya ke sha ba. Tun yana kyankyami har ya zamo masa jiki. Don ka'ida ne kullum ta Allah ya zo gaishe ta, sai ta cika kofi ta ba shi tsawon sati biyu suna hakan. Ya ji ya fara jin wasu sauye-sauye a zuciyarshi akan Mairo, sai dai ko kusa bai alakanta hakan da cewa rubutun da Hajiya ta ke daddaka masa ba ne. Yau da yamma da ya dawo daga ofishin Daddy inda ya koma zuwa yana taya shi da wasu ayyukan, sabida nauyin Habibu da yake ji ya sanya alakarsu yanzu ta ja baya. Duk da cewa shi Habibun a nashi bangaren, ya maida komi ba komi ba, amma Amirun gani yake Hajiya ta riga ta gama tozarta shi a idon Habibu, ta yadda har abada ba zasu koma kamar da ba. Ya yi sallama Hajiya da ke harde cikin kushin tana sauraron labaran Al-Jazeera ta amsa mishi. Ya samu kujera mai fuskantarta ya zauna. Ya dan zamo daga cikin kujerar yana gaishe ta. Ta amsa mishi da sakakkiyar murya, can kuma ta ce. "Anya Amiru, rayuwa zata yiwu da hakan? Ace mutum ya yi ta zama, ba ya tunanin samun dan kansa, duk tsararrakinka daga masu 'ya'ya uku sai masu hudu amma kai ba abin da ya dame ka, sabida idonka ya rufe da son matarka. Alhalin kuma ba zata iya ba ka sanyin idanu ba, sai dai a cika maka masai da kashi, to wallahi bazan yarda da wannan ba". Ya dago idanunshi a kankance ya dubeta. "Hajiya mun isa mu ba wa kanmu abin da Allah bai ba mu ba ne? Sannan ba ki san matsalar nan daga gare ni take, ko daga gare ta ba? Don haka bai kamata ki dau zafi akan al'amarin ba, don Allah Hajiyata". Ta ja dogon tsaki tsiiit! "To ku je asibiti mana? Ko haka za mu yi ta zama cikin jiran gawon shanu? Ai gara a banbance, don a san matakin dauka". Da wannan tunanin na maganganun Hajiya ya kwana, har ya soma jin kamshin gaskiya a cikinsu. A shekarunshi ya ci ace shi ma ya aje masu yi mishi addu'a. Har ya soma zargin Mairo ko tana amfani da 'contraception'. Tunda dama ai tun farko ba sonshi ta ke yi ba. Ya yi gaggawar kwabar zuciyarshi daga wannan mummunan zargin da ta darsa mishi. Ya yarda da matarsa 100% (Azzannu zambun, wa lau kana hakkun), sai dai rashin damuwarta akan al'amarin ma ai abin dubawa ne, bokonta kawai ta sa a gaba, da son ganin kwalayen ilimi, tare da son hango kololuwar biro da takarda. Ta murda kofar ta shigo cikin sallama cikin sassalkar doguwar riga baka sid, kirar Dammam, fararen duwarwatsu na ta walwali a jikinta, sannan ni'imtaccen kamshinta na din-din-din ya doki hancinsa. A kwance yake 'flat' bisa makeken gadonsu ya lumshe ido kamar mai barci. Har ta zauna gefen kafafunshi ta soma ja mishi yatsu bai juyo ba. Haka nan ya samu kanshi da jin haushinta babu gaira babu dalili. Ta yi kiranshi cikin tattausar murya, amma bai bude idonshi ya dubeta ba. Karewa ma kara runtse idonshi ya yi, tareda janye kafarshi dake ciin hannunta, don ba ya son ganinta, ba ya son kamshin turarenta. Ta yi wa kanta kyakkyawan matsugunni a kirjinshi, ji ya yi kamar ta dosana masa wuta. Ya yi azamar angijita ya ce "Leave me alone, please!" Cikin mamaki ta ke dubanshi, idanuwanshi sun hargitse kamar ba Amirun nata ba. Ta ja gefe ta zauna jikinta yana rawa, don ko kadan bai taba yi mata magana cikin tsawa irin haka ba, sannan ita a rayuwarta ba ta iya tashin hankali ba. Zuwa can kuma ya mike ya soma shiri, ya dan juyo a kai-kaice ya kalle ta. "Ki shirya, asibiti za mu". Ta yi ta maza cikin sanyi ta ce. "Waye ba lafiya?" "Idon matambayi ne". Abin da ya ce da ita ke nan. Kamar ta ce, 'to ba zani ba', amma kwarjinin Amirun da kimarshi dake cikin idanunta ya hana. Soyayyar da ta ke mishi wata kaddara ce daga Allah da ita kanta bata san adadin ta ba. Ta yadda ba ta iya fushi da duk abin da ya yi mata. To balle ma bai taba yin ba. Idan haka ne ya dace ta yi mishi uzuri, ba kullum ne mutum yake kasancewa cikin dadin rai ba. Suna tafe a motar amma ba mai ce da dan uwansa uffan, kowanne abin da yake sakawa a zuciyarsa daban ne da na dan uwansa. Tunanin Mairo shi ne, shin laifin me ta yi wa Amiru haka da zafi, da har ba zai iya budar baki ya fada mata ba don ta gyara? Shi kansa Amirun ya rasa laifin da ta yi mishi ya ke ganinta bakikkirin da jin zafinta babu gaira babu dalili. Amma ransa na gaya masa rashin haihuwar tane, yazo wani limit na kasa jurewa. Har suka iso babban asibitin Abuja, kalma daya ba ta hada su ba. Kai tsaye ofishin Dr. Fredrick suka nufa, Amiru ya ce da shi. "Doctor mun zo ne yau ka duba mana dalilin rashin haihuwarmu, al'amarin ya fara damuna. Sannan Hajiya ta tada hankalinta, idan ba asibitin nan muka zo ba, ba zata barni na zaun lafiya ba". Sai a sannan ne Mairo ta cira ido ta dube shi. Yanzu ne ta gano dalilin bacin ranshi. Wato sun fara damuwa da rashin haihuwarta, wanda ita ba ta isa ta bai wa kanta ba. Dr. Fredrick ya hada su da Gynaec Doctor da za su gani, wato Dr. Ma'u. Bincike iri-iri Dr. Ma'u ta yi amma ba ta gano wata matsala a tare da Amiru ba. Da ta zo kan Mairo, sakamako ya nuna cewa, ita ce bakin mahaifarta yake a tsuke sosai. Idan har tana son haihuwa, dole sai an yi mata aiki, an bude bakin mahaifar. Ya roki Dr. Fredrick da Dr. Ma'u lokacin da Mairo ta nufi mota cewa su taimake shi su bar wannan sirrin a tsakaninsu, ba ya son Hajiya ta ji. Dr. Ma'u ta ce da shi. "Ai ko ba ka ce ba, amana ce tsakanin likita da 'patient' dinsa, insha Allahu ba za a fada mata ba". Ya yi godiya ya barsu da alkawarin idan sun dai-daita ranar da za a yi mata aikin za su dawo. Mairo ta shiga cikin tsananin damuwa. Tashin hankali da rudani. Yadda farat daya Ameeru ya sauya mata. Kamar ba shi ba. Babu wannan murmushin, babu wannan soyayyar tashi mai kidimata. Kullum daga fada sai hantara. Duk ta bi ta kare a tsaye, ta soma samun tangarda a karatunta. Amma don zurfin ciki irin nata, ko Dina ba ta taba tunanin fadawa ba. Hajiya ta samu yadda ta ke so, domin ta janye hankalin tilon danta kanta. Duk abin da ta ce da shi dashi ya ke amfani, jikin shi har rawa yake wajen bin umarnin ta, ta himmatu da yi wa surukarta karfar baka, mai wuyar magani, wadda ta fi kiyayyar zahiri lahani a zuciyar wanda ake mawa. Duk yadda ya so ya lallame ta su koma asibiti a yi mata aikin amma Mairon ta ki. Idan ya takura mata da nacin maganar sai ta sa kuka. Ga shi shi kuma ba abin da ya tsana irin kukanta da ke soya zuciyarshi. Ta dage akan cewa, ita Allah ne kawai bai nufe ta da samun cikin ba. Ranar da ya nufa Ya ga damar ba ta zata samu ne. "Amma Shi Ya ce 'tashi in taimake ka. Sannan babu cutar da Ya saukar ba tare da ya saukar da ita tare da maganinta ba. Idan ke ba ki damu ba, ni ina son ganin dan kaina. Tun da rayuwar ba jiranmu ta ke ba, mu muke jiranta". Tana so ta yi tsaki, amma kimarshi da martabarshi sun wuce hakan a idanunta. Dole ta maida tsakinta. "Ni fa babu inda zan je". Duk inda ranshi yake idan ya yi dubu, to ya baci. Ba ta taba yi mishi musu a rayuwarshi irin na wannan lokacin ba. Ya rasa abin da zai mata YA HUCE... Gaba daya ya soma tunanin bokon da ya barta tana yi ne ya sanya ta raina shi... Wannan ne karo na farko da ya kai kararta wajen Habibu tun bayan aurensu. Habibun ya ce, ya kawo mishi ita. Daga ita sai Yaya Habibun a babban falonshi, don Amirun da ya kawota bai zauna ba ya wuce ofis wajen Daddy. Dina na kicin tana kacaniyar shirya abinci. Habibu ya ce "Mairo me nake ji haka? Wai mijinki bai isa ya sa ki abu ki yi ba? Idan ke ba kya son 'ya'yan, to shi yana so. Muma muna so, me kike nufi da ba zaki yarda a yi miki aikin ba?" Ta fashe da kuka, ta ce "Da da ne ya ce na yi abin da yake so, ai zan yi ne, ba tare da kowa ya ji ba. Amma ni ma yanzu ban san me yake nufi da ni ba. Babu magana mai dadi tsakanina da shi sai hantara. Kuma yadda ya ke nunawa kamar ta karfi yake so na haifo mishi dan, sannan ni gaskiya tsoro nake ji, lafiyata kalau inje a jagwalgwala min mahaifa". Habibu ya ce "Likitoci ba za su yi miki karya ba Mairo. Maganar canzawarshi sai ki yi mishi uzuri, yanayin rayuwar kenan, wata rana a sha zuma, watarana a sha madaci! Ba kullum ne mutum yake kasancewa cikin dadin rai ba!". Da kyar Habibun ya rarrashe ta, ta yarda za su je ayi aikin. Ranar litinin Dr. Ma'u ta yi mata aikin. *** Tsawon shekara guda har da doriya, babu wani bayani, wato ba abin da ya sauya bayan yin aikin. Babu ciki ba alamarsa. Dai-dai lokacin da ta kammala rubutun 'project' dinta na kwalin master, sabida kwazon da ta nuna kai tsaye suka ba ta gurbin zama daya daga cikin malamansu, wato 'lecturing' a jami'ar Abuja. Mairo ta debi kudi masu yawa, ta dankawa Yaya Habibu aka soma ginin makarantar firamare da sakandire a kauyen Gurin-Gawa. Sannan ta dauki sauran gaba daya ta mallaka mishi halak-malak, bayan ta warewa Baffa nashi kason. Habibu ya saida gidanshi na kasar America da wasu manyan kadarorinsa ya tada kafadar (Habib Bank) wanda ke gaf da durkushewa. Cikin taimakon Allah sai al'amuran suka soma dai-daita. Amma a ranshi ya dai karbi kudin Mairo ne kawai bai ce mata komi ba, sai dai cikin ranshi ya kudurce juya mata zai yi. *** Hanan Abdulwahab, diyar kanin Hajiya ce, wato Uncle din Amiru da ke garin Gaya. 'Yar kimanin shekaru ashirin da hudu, kyakkyawa ce matuka, kuma tana da irin tsagin su Amiru a gefen hagu da dama na fuskarsu. 'Yan asalin garin Gaya ne su ma, don da Babanta da Hajiya ubansu daya. Mahaifinta tsohon soja ne, wanda ya rike manya-manyan mukamai a aikin soji, har zuwa matsayin da yake kai a yau, wato Major Genaral Abdulwahab Gaya. Gaba dayan karatun Hanan tun daga firamare har jami'a ta yi shi ne a garin Lagos, inda mahaifinsu ya yi aiki a wancan lokacin. Daga baya da ya yi 'retire' suka dawo garin Kaduna da zama, inda suke zaune a halin yanzu. Direban Hajiya Mr. Kademi ne ya je ya dauko Hanan daga filin jirgi, wadda ta sauka karfe hudu dai-dai na yammacin ranar ta Laraba. Hajiya ta yi mata kyakkyawar tarba bayan ta rungumeta tana lale da diyarta. Kamar yadda Hajiyar ta nemi izinin mahaifin Hanan di n kan ya barta ta zo ta yi mata kwana biyu. Sun baje a falon Hajiya suna labari, Hanan ta ce. "Ina labarin brother, yanzu yaran shi nawa ne Hajiya?" Hajiya ta kyabe baki, ta ce. "Babu ko daya". Hanan ta yi murmushi, ta ce. "To ai kin san Turawa ne, watakila ba su shirya fara tarbar 'ya'yan ba". Cikin rashin walwala Hajiyar ta ce. "Ke raba ni da abin haushi, kada ke ma ki bata min rai yanzun nan. Turancin yaci abu kazan ubansa. Ba wani tsarin iyali, juya kawai ya je ya auro". Kwanan Hanan biyu a gidan, amma ba su hadu da Amiru ba, sabida sanda yake shigowa gaida Hajiyar da safe ita ba ta tashi daga barci ba, sabida dai Hanan 'yar hutu ce ta karshe. A rana ta uku ne da ya shigo Hajiya ta je har dakin da ta sauka wanda ya kasance dakin su Rayyah ne kamin su yi aure, ta tasota ta ce ta zo su gaisa da Yayanta. Ta ba ta wani farin kwalli ta ce, ta zizara a idonta, ta yi duk kokarin da zata yi ta tabbatar sun hada ido. Hanan ta cika da mamakin mene ne dalilin Hajiya na yin hakan? Sai dai kuma ba ta jin zata iya kin bin umarnin Hajiyar. Tsaye ya ke a baranda yana amsa kiran Habib cikin wayarshi, a lokacin da Hanan ta fito falon. Ya juya baya hannunshi daya dafe a bayanshi, yayin da ya yi amfani da dayan wajen rike wayar. Hanan ta tsura mishi idanu, wani al'amari mai karfi na fizgarta. Rabonta da Amiru tun wani zuwa da ya yi Kaduna gaida mahaifinta a lokacin yana Washington. Zuwa yanzu ya kara girma da haiba. Duk wasu kamanni na ingarman namiji ya mallake su, kuma kyakkyawa na karshen-karshe. Ya zama 'giant' mai wani irin kyawun halitta na burgewa da ban mamaki. Irin mazan da ba kowacce lafiyayyar mace ce zata iya dauke ido a kansu ba. Gwiyoyinta suka yi sanyi, kuzarin jikinta ya kare, wata irin soyayyar Amirun na tsirga zuciyarta. Ba ta iya ta dauke ido a bayanshi ba har ya juyo. Da farko kallo daya ya yi mata, amma ya rasa dalilin da ya sanya ya kasa dauke idonshi a kanta. Don sai ya ganta kamar Mairo, idanunta, bakinta da karan hancinta duk sun rikide sun koma na Maironshi sak! Har ya ke jin yafi son wannan Mairon, akan wadda ya baro a gida. Sakon Hajiya ya yi aiki sosai, ya hada wata matsiyaciyar soyayya, mai wuyar fassarawa. 8/8/21, 1:23 PM - Kawata: 55 Tsayin watanni biyu Alh. Abdurrahman na jinyar tilon dansa, ya na kwantar masa da hankali ta hanyar bashi misalai da al’amuran rayuwa kala-kala. Don ya yaye wa kanshi damuwar daya sanyawa zuciyar shi. Yana kuma karantar abubuwanda ke faruwa a cikin gidanshi musamman Hajiya A’isha daya digawa gundumemiyar ayar tambaya. Sabida yadda ta fita hayyacinta da rashin lafiyar Amiru, sai surutai take mai tonawa kai asiri, wani zubin ta hada da su Nina tace su suka angizata, ta zazzagesu tayi musu mugun kalami tana cewa sun cuce ta. Bai tambayeta komai ba, kuma bai tambayi Amiru mai yasa ya saki Mairo ba. Wanda rayuwar sa ke hannun Allah. Dr. Fred yana zuwa gida akai-akai yana kula dashi. Ya ki yarda a maida shi New-York. Yace da Daddy in ma mutuwarce, to yafi so ta dauke shi a dakin da yayi rayuwa da Mairo. A yau Ambasadan Malaysia yazo ganin sa, ta dalilin Habibu da Amiru Daddyn Dina da Alhaji Abdurrahman suka kulla abota. Alh. Abdurrahman yayi masa kyakkyawar tarba, shikansa saida ya zubda hawaye ganin halin da Amirun ke ciki. Ya koma Malaysia cike da alhini inda ya tarar da Mairo da tata sabuwar matsalar har yau ba sauyi. A wannan satin da surutan Hajiya suka ishi Alh. Abdurrahman, yayiwa ‘ya’yan shi mata gabadaya waya, na ciki dana waje, yace yana so su hallara a ‘family meeting’ ranar asabar mai zuwa. Sannan ya kira Alh. Abdulwahab Baban Hanan shima yace yana so Hanan tazo ranar asabar. Alhaji Abdulwahab wanda ke cike taf da fushin sakin da Amiru yayiwa Hanan sati daya da aure ya gintse fuska yace “ince ko lafiya? Bayan an riga an saketa?” Daddy yace lafiya kalau, ‘meeting’ zasu yi tare da ita. Ya gaya mishi bai san abubuwanda suke faruwa a gidan ba, yana so ya sani ne, inda halin gyara ayi gyara. Yace Hanan zata zo albarkacin ka, amma babu batun gyara. Don dama Hanan tana da mai sonta tuni, mutunci da ‘yan uwantaka aka diba aka bawa Amiru. Tunda kuma yace baiyi, to Allah ya hada kowa da rabonsa na ALHERI. Jikin Daddy a masifar sanyaye, da mamakin wai itama Hanan an saketa. To shi yana ina aka yi duk wannan kazamin aiki? Lallai Hajiya ta bashi mamaki. Ya kuma soma zargin koma menene itace ummul-haba’isi, haka kawai za’a kashe masa Da a banza. Habibu bai bar jinyar Amiru ba, duk da tabbacinsa na sakin Mairo da yayi. Duk da zafin hakan dake ranshi. Duk wai wata kusan tafi wata kusan. A wurinshi ba Mairo ce ta hada shi da Amiru ba balle ta zamo silar rabuwarsu. Allah ne ya hada su, ya sanya kaunar juna da soyayya a tsakaninsu, ba kuma zasu rabu a dalilin ta ba. Ko ba komai Amiru ya wanke mishi zuciya da baiyi mummunan saki ba wanda Allah baya so. Yayi kokari ya karanta hargitsatstsen rubutun ya ga saki daya ne. Kullum kafin ya fita ofis zai zo, haka in ya tashi yana nan tare dashi har goman dare. Amiru yana shaida kowa, amma baya magana. Sai bin kowa da ido. A ganin shi rayuwar bata cancanci a cigaba da itaba, ba tare da abinda zuciya da gangar jiki ke so ba. In za’a bashi zabi gara mutuwa da rayuwa babu Mairo. Kasancewar Daddy da Habibu na kula da shan magungunan sa akan lokaci, ya sanya kullum sauki na kara samuwa. Daddy ya shigo falon da ‘ya’yan sa, Hajiya da Hanan ke zaune, kowanne kai a kasa. Jiki yayi la’asar babu laka. Ita kanta Hanan ta tsorata da ganin yadda Amiru ya koma cikin dan lokaci kalilan. Sau daya ta shiga part dinshi, tausayi bai barta ta kara komawa ba. Ko babu soyayya Amiru dan uwanta ne wanda take ji har cikin kashi da bTa kuma alkawartawa ranta fadiwa Daddy gaskiyar duk abinda ya tambayeta ba tareda shayin Hajiya ba, don Yaya Amiru ya samu lafiya, ya samu abinda yake so, ita tayi hakuri, ta auri Ramadan wanda ke son ta kamar ya kashe kan shi. Amina kadai ake jira a falon wadda bata karaso daga Switzerland ba har yanzu. Don haka ganin ana batawa ‘majority’ lokaci, akan mutum daya, Daddy ya yanke hukuncin ayi taron bada ita ba. Ya bude taron da cewa kowa yayiwa Annabi salati goma. Ya ja doguwar addu’a suka shafa. Yasa gilashi ya soma duban ‘ya’yanshi mata su goma sha daya da fuska mara walwala. Ya maida dubanshi ga Hajiya A’isha yace “Hajiya, keda Hanan kune a gidannan sanda abin ya faru, don haka ku zan fara tambaya. Yaya aka yi Amir ya saki matansa biyu duk a lokacin daya?” Hajiya tayi shiru, ta soma share ido da gefen mayafinta, abinda ya riga ya zame mata jiki tun ranar da aka dawo da Amiru wai yana fama da ciwon zuciyar data yi tsammanin yayi hannun riga da shi. Tararradinta shine idan ta rasa Amiru ina zata tsoma ranta? Mutumin da ke yi mata biyayyar da duk cikin ‘ya’yan ta babu mai yi mata kwatankwacinta? Mutumin da ya sadaukar da farin-cikinshi akanta. Bama wannan ba, ina zata kai hakkin Mairon da bata ci mata ba, bata sha mata ba, biyayya take yi mata tamkar tayi mata sujjada, kawai don Allah As-samadu bai bata haihuwar da bata isa ta baiwa kanta ba? Ta tabbatar ba komai ya kai ta yin umarnin data yi ba, bacin ran sakin da yayiwa Hanan ne. Wadda ita bata damu ba, kamar dama jira take, yana sakinta ta hada ya-nata-ya-nata tayi tafiyar ta, babu ko cikakkiyar sallama. Sai yau ta ganta cikin taron da bata zata ba. Amma ko waya Hanan bata kara yi mata ba. Gatanan da ranta da lafiyar ta ba abinda ya dameta. Sai nata dan data jefa cikin halin ha’u’la’i. zaiyi-ba zaiyi- ba Allah masani. Ta dubi Nina, kamar ta tsinka mata mari, domin dai ita ta kaita ga abinda bata taba tsammanin yi a rayuwarta ba. Wato bin malaman tsafi Yarbawan Lagos, haka-kawai zasu fidda ita a imanin ta. Kukanta ya tsananta ta kasa baiwa Daddy amsa. Don haka ya juya akalar tambayarsa ga Hanan. Ta sunkuyar da kai ta soma fada masa duk abinda ya faru, tun ranar da Hajiya ta aika ta zo, abubuwanda ta rinka bata wai tayiwa Amiru amfani dasu, har zuwa ranar daya saketa, da tirkeshi data yi ya saki Mairo. Daddy ya jinjina kai cikin al’ajabi da mamaki, yaushe Hajiya ta koma haka? Ya ce da Hanan ya gama da ita, kuma ya gode. Kuma menene ra’ayinta kan zama da Amiru? Tana so idan Allah Ya bashi lafiya zata dawo dakinta ne ko a’ah? Ta sunkuyar da kai tace “ka fahimce ni Daddy. Ba wai bana son Yaya Amiru ba, amma shi wallahi-wallahi baya so na. Matarshi kadai yake so Daddy. Kuyi kokari ku dawo mishi da abarshi cikin gaggawa in har kuna son lafiyar shi fakat. Nikam har ga Allah na hakura, zan auri mai so na. Daman kuma babu iddarshi a kaina”. Daddy ya sake jinjina kalamanta, yayi mata godiya ya sallameta ta fita ta koma wurin Amiru. Inda aka baro su shida Habibu. Daddy ya dubi Hajiya cikin wani irin fushi da ‘anger’ da bata taba gani daga gareshi ba. Fuskar shi tayi jawur abinki da bafulatani, jijiyoyin kansa sun fito rada-rada, idanunshi sun canza launi daga farare sol zuwa jajaye. Jikinshi na tsuma, tsigar jikinshi na tashi yace “A’isha! Hanan gaskiya ta fadi ko karya ne?” Ta juya kai cikin tsoro da tashin hankali, nadama da yin kaico da kai, don bata taba ganin shi cikin wannan halin ba. Tace “batayi karya ba anyi haka. Sai dai kuskure ne da ajizanci irin na kowanne dan adam. Na tuba Alhaji na bi Allah na bika. Sai dai komai ya faru ne da zuga da taimakon wadannan……….” Tana nuna Nina, Ni’ima da Khalisa. “Su suke karbo komi a Lagos wallahi ban taba zuwa ba. Don nasan zuwa wajen irin wadannan mutanen haramun ne. Na roke ka, kada ka bari Habibu yaji wannan magana don GIRMA NA ZAI FADI A IDANUN SA don ba iyakarta kenan ba…….” Cikin nishi Alh. Abdurrahman yace “sai kuma me?” Ta yarfe hawaye da majina tace “Na sanya shi ya janye hannun jarinsa daga bankinsu shida Habibu……duk takardun dukiyar shi suna hannu na yanzu, bari inje in dauko…”. Tana shirin mikewa ya daga mata hannu “bayan Nina, Ni’ima da Khalisa sai kuma wa?” tace “sai mutanen Gaya. Su suke cewa “juya” ce. Don haka ne na kulla auren shi da Hanan don ya samu ‘ya’ya kawai wallahi, amma ba don in raba shi da matarsa ba….. kai shaida ne akan cewa tsakani da Allah ina son Mairo”. Ya kalli Nina da Khalisa da suka yi tsuru-tsuru, jikinsu sai kyarma yake. Don sun gigice da ganin ‘tension’ din mahaifinsu mai son su da gudun bacin ransu, tareda kyautatawa rayuwarsu tun daga yarinta har girma. Rayyah tace “wallahi babu ruwana……” Sabah tace “wallahi babu hannu na…..” Mami tace. “ni Daddy da ba a kasar nake ba, wallahi bani da masaniyar komai…….”. Juyawa yayi gefensa ya fizgo wayar talbijin. Ya soma binsu yana tsula musu. Duka na tashin hankali. Da masu ruwan, da wadanda suka ce babu ruwan su. Yana hawaye yana tafkarsu, yace “Kun yi asara! Kun kashe auren mutumci da amana da soyayya ta gaskiya!! Bazan yi muku baki ba. Amma kuji tsoron hakki. Kuje duniya kadai ta isheku, tunda kuma mata ne kuma aure kuke kamar yadda Mairo ke zaman aure. Sannan abinda kuka yiwa Mairo, kuka sa aka yi mata, zai iya faruwa da kowaccenku. Dan uwanku kuma idan yana da hakkinku Allah zai fitar masa, muddin ya mutu bai yafe muku ba. Kuma sai kun maimaita wannan magana agaban Habibu, sai Habibu yaji wannan maganar. Ke kuma Hajiya ki tattara ya-naki-ya-naki ki tafi Gaya, sai na nemeki…….bana bukatar ganin ki a cikin gidana yanzu……”. Kowa a falon kuka yake, yana rokon gafara. Basu kara tsananta kukansu ba, saida suka ji wannan danyen hukuncin da Daddy ya zartas akan Hajiya. Suka rirrike kafafun shi suna bashi hakuri yace “ni baku yi min komai ba. Wadanda kuka yiwa su zaku nema gafara amma ba ni ba. Sannan bazan taba sanya baki Mairo ta dawo gidan dan uwanku ba. Tunda bakwa son ta. Ku aura mishi duk wadda kuke so tazo ta cika muku gida da ‘ya’ya. Ko ya mutu, ko yayi rai, na barwa ALLAH! Ku bace min da gani dabbobin banza. Hajiya ina kara gaya miki, kada in dawo in ganki cikin gida na….”. Ya yarda wayar ya fice, yana share hawayen da suka cika mishi ido. *** Wasa-wasa sai da Mairo ta kwashe watanni uku cur cikin wannan halin, a lokacin cikin jikinta ya fito sosai, domin ya shiga cikin watanni na biyar. Rannan daga ita sai Hajiyar Dutsinma a dakin, ta farka daga barci, ta kurawa silin ido, al'amuran suka soma dawo mata tar-tar. Ta tuna wai Amiru ya sake ta, ba tareda ta yi mishi laifin komi ba, alhalin suna tsaka da son junansu. Bayan ta mallaka mishi duk wata soyayyarta. Sannan ya auro Hanan, ba ta fita daga wannan bacin ran ba, ya dankara mata saki, ta tabbatar bisa tursasawar Hajiya ne, amma Amirun ba zai taba yi mata haka akan-kanshi ba, ko giyar wake ya sha. Tana mai sa ran bada jimawa ba za su dai-daita da mijinta ya maida ita ta zauna lafiya da Hajiya Aisha, tunda abin da Hajiyar ta kwallafa rai, har ta tsane ta a kanshi, ga shi Allah Ya bayar. Sai kuma ta tuno wai an fada mata ya kara kamuwa da ciwon zuciya irin wanda yayi a baya, aka samu rayuwarshi da kyar da taimakon ta. Gashi yanzu basa tare. Kai ita ji tayi ma kamar ance ya rasu! Daga bakin Hajiyar Dina da ba zai taba yi mata karya, ko zolaya ba. Ta soma kuka a hankali, kukan sabo, soyayya, kauna da kewa. A tsayin zamansu na shekaru takwas, bai taba bata mata ba, sai bisa kuskure. Soyayyar da ya wanzar da rayuwarshi a nuna mata, wani abu ne da ba zai taba kankaruwa daga zuciyarta ba. Tunda ya aure ta ya haramtawa kanshi sauran mata. Bai kara hada jiki da wata diya mace ba, bayan ita, har inda yau ke motsi. Har kuwa wadda ya aura da auren sunnah. Taji wannan a bakin Hanan ba a bakinsa ba. Duk da matakin rayuwa irin nashi, wannan bai shagaltar da shi daga rudin duniya ba. Ta tabbata ta yi babban rashin da har abada ba zata mayar da makwafinsa ba. Ta mika hannu ta shafi kasan mararta, inda babynshi ke kwance, yana wutsil-wutsil cikin koshin lafiya. Ta lumshe ido a hankali, hawaye masu dumi suna zirara ta gefen idonta suna shiga cikin kunnuwanta. Ba ta damu da ta share ba, haka zuciyarta ba ta daina kokawa ba. A wannan halin Habibu ya tarar da ita. Ya ja kujera ya zauna yana fuskantarta. Ya ce. "Mairo, Mairon Dina, Mairon Yaya Habibu..." Ga mamakinshi sai ta fado jikinshi tana kuka mai tsuma zuciya. Ta ce. "Yaya Habibu da gaske mun rasa AMEERU?" Ya ce "Mun rasa auren shi dai Mairo, da gaske mun rasa auren mai kaunarmu da gaskiya da amana. Amma Ameeru yana nan a raye. Duk wanda yace dake ya rasu, ya fada miki ne kawai don ya tayar da hankalinki. Ko kuma baki tsaya kin saurara dai-dai ba. Amma yana gida, kwance a dakin ki. Akan gadon ki. Kwanciyar shi ciwo da rabuwar auren ku ya barni da kewa, da katoton gibi a zuciyata. Wanda mayar da shi wani abu ne da ba zai taba yiyuwa ba. Don haka ki dage da yi mishi addu’a. Allah ya bashi lafiya cikin gaggawa. To lose a friend like him, will be the GREATEST lose of all losses. To lose a husband like him, is another GREAT loss. (rasa aboki kamar sa, ba karamar asara ba ce daga manyan asarori, kuma rasa miji kamar sa, shima babbar asara ce.) Sai dai mu cigaba da yi mishi addu'a. Allah ya bashi lafiya. Wannan ne kadai babbar sakayyar da zamu yi wa masoyi irinshi. Amma ba da son ranshi ya sake ki ba. A matsayinmu na musulmi, ma'abota imani da yarda da kaddara, muna da tabbacin cewa, duk abinda ya faru damu da sanin Allah. Shine mai sanya cuta, kuma shine mai yaye ta. Don haka muna da kyakkyawan zaton Zai tashi kafadar Amiru, a lokacinda ya so. Ya cigaba da gudanar da al’amuran kyakkyawar rayuwarshi. Inda rabon zaku komawa auren ku, to da yardar Allah zaku koma. Amir bai yi haka ba Mairo, sai bisa tirsasawa. Ya kamo hannunta ya rike cikin nashi, ya ce. "Mairo mun rasa Baba, mun rasa Inna, amma mun hakura kan ba yadda za mu yi. To haka da muka rasa auren Amiru, zamu yi hobbasar yin tawakkali. Mu ci gaba da jure jarrabawoyin da Ubangiji ke yi mana a rayuwa, har mu cinye jarrabawarmu. Don haka ki yi hakuri kamar yadda na yi hakuri, iyayenshi da 'yan uwanshi suka yi, kan halinda yake ciki. Kuma Alhamdulillahi yana gane mutane yanzu saidai ya ki asibiti. Hajiyar Amiru dasu Nina suna can suna ta nemanki, suna neman inda za su ganki su nemi gafarar ki sun rasa. Ta yi nadama/sunyi nadamar abin da suka yi mana. Yafiyarki su ke nema Mairo. Afuwata suke nema da hawayensu. Sun gurfana kan gwiwoyin su a gabana don na yafe musu. Sannan sun samu Daddy sun bayyana mishi duk abinda suka yi mana, yayi mamaki nima nayi mamaki, ya saba musu sosai kuma sunyi nadama ta gaskiya akan ki Mairo. Yace dasu ai ga sakayya nan sun soma gani tun a duniya, tunda Amirun na neman rasa ransa a kanki. Wallahi Mairo tun bayan tafiyar ki ko kofar gida Amiru bai kara takawa ba, yana gidan ki, daga dakin ki sai falon ki. Hajiya in kin ganta a halin yanzu dole ki tausaya mata, watanta daya a Gaya ya koreta, kiris ya rage ya saketa saida nasa baki tukunna ya hakura. Ta ce ki yi wa Allah ki kula mata da abin da ke cikinki. Sabida na gayawa Daddy kina da ciki shikuma ya gaya musu. Sabida haka ki kwantar da hankalinki, don a samu daidaituwar B.P dinki, don hawan jini hatsari ne ga mai juna biyu, kuma jininki ya hau, don haka ki taimake ni Mairo, kada kema na rasa ki……...bani da Uwa, bani da Uba, sai ke da abinda zaki haifa…." Hawaye sharrr! Suka zubo daga idonsa. Ta kai hannu tana share masa, ita ma nata suna zuba. Cikin rishin kuka ta ce. "Ka daina kuka Yaya Habibu, na yi maka alkawarin zan kwantar da hankalina tunda yana raye". Ya ce, "To tashi ki ci abinci, ko dan cikinki ya samu. Bai kamata ki dinga zama da yunwa ba, plzzz... Mairona!". Ta ce "To ba ni in ci". Ya bude kular da ke gabanta, ya zuba mata faten dankalin Turawa, wanda ya ji tsokar naman kaji ya yi lugub. Ya mika mata a faranti, ya cika tambulan da (fresh milk) mai sanyi ya mika mata. Ta karba ta soma ci sosai har tana taune harshenta sabida yunwa. Dina ta shigo rike da kwandon kayan abinci, suka zauna akan kilishi suna ci ita da Habibu. Mairo na kallonsu tana raya abubuwa a ranta, wato ranar da aka kaita gidan Amiru ya takura mata sai ta ci abinci akan idonsa. Ta kai hannu da sauri ta goge hawayen da suka kara shimfido mata, don ba ta son Yaya Habibu ya gani, ranshi ya baci. Amma ta riga ta san kuka ta dinga yinshi kenan, har karshen rayuwarta. Tunda yanzu itada Amiru sai dai a TUNA BAYA……Yaya zatayi da dimbin soyayyar shi data kankanewa zuciyarta???? An sallami Mairo ranar wata asabar bayan likitocinta sun tabbatar komi nata ya koma dai-dai. A lokacin cikinta ya cika watanni shidda cif, wanda ya yi dai-dai da cikar Amiru watanni hudu yana jinya. Suka dawo gidan su Dina, inda a washegari Habibu da Dina suka yi shirin tahowa gida Najeriya. Gidan ya rage daga Mairon sai Hajiya da masu aiki, don Abban Dina bai cika zama ba sai a weekend, kullum yana ofis. Bata tashi daga inda ta yi sallolin farilla guda biyar, ba tareda ta yiwa Amiru addu'ar neman lafiya daga Ubangiji ba. Hajiyar Dina na kula da ita yadda ya kamata, ko Innarta iyakacin kulawar da zata yi mata kenan. Watan Hajiyar Dutsinma biyu tare da su jikinta ya yi kyau ta koma gida. Kwanaki na mirginawa su zama watanni, har watan Aprilu ya kama, wanda shi ne EDD dinta. Sai dai Mairo ba ta yarda anyi mata ‘scan’ ba. Ranar wata alhamis nakuda ta tashi cikin dare, haihuwa gadan-gadan. Don haka ba da bata lokaci ba Hajiya ta tuka su da kanta suka nufi asibitin da ta ke awo, nan da nan aka karbe ta a (labour ward), nakuda ta tsayin awanni uku cur, kan Hassan ya bullo, kamin likitocin su yi wani yunkuri, shi ma Hussaini ya biyo dan uwansa. Aka turota dakin hutu, Hajiya na rungume da jariran tana yi wa Allah sarkin halitta tazbihi, sabida kamar Amiru ya yi kaki ya tofar. Sannan ‘identical twins’ irin wadanda banbacesu zai yi wuya. Sai dai da alama Hassan kalar Babanshi ne, wato (choculate), yayin da Hussaini ya debo hasken fatar Mairo. A take Hajiya ta yi waya ta sanar da Habibu, ya yi hamdala ya kuma nemi wayar Alh. Abdurrahman ya sanar da shi, don haka a karshen satin suka dungumo har Hajiyar Amiru dasu Sabah suka iso Malaysia. Farin ciki a wajen Hajiya Aisha da Alh. Abdurrahman abin ba’a cewa komi. Hajiya har da kukanta na nadama, ga dai ‘ya’ya ba daya ba har biyu Mairo ta Haifa, duk kunyar Mairon ta isheta, ta kama 'yan jikokin ta rungume tana yi musu addu'a, ji take kamar Amirun ne ta rungume a ranar data haifeshi, sai dai dukkaninsu babu mai ra'ayin a yi wani taro sai addu'a da kowa yake yi wa mahaifinsu, wanda har zuwa lokacin ke kwance cikin halin jinya. Yara sun ci sunan Habib da Amir, babu kuma wanda ya yarda da a sakaya. Ana kiransu da sunansu abinsu. Bayan su Hajiya sun koma Mairo ta ci gaba da rainon 'yan biyunta cikin koshin lafiya da taimakon (Nanny) Bamaleshiya da Hajiya ta daukar mata. Kamin watanni hudu sun cika sun yi kiba, sun yi bul kamar 'yan watanni goma sabida samun kulawa da ruwan nono isasshe. A lokacin ne kuma 'addmission' dinta na yin PhD ya fito a 'university of Malaya'. A satin da zata fara karatu, Yaya Habibu ya zo Malaysia. Yace tayi shiri suje Najeriya ta kaiwa Amiru ‘ya’yan shi ya gansu. Don ya samu sauki har ya soma zuwa ofis. Daddy ya samo mishi aiki a CBN. Don shi Habibun bai yarda su sake yin hadin gwiwar ba kamar yadda Daddy da Amirun suka bukata, yace saboda halin rai. Ya kuma ce da Daddy akwai kudurin da yake dashi a kan bankin nan bada jimawa ba. Amma ba wai don yayi fushi da abinda Hajiya tayi ba. Mairo bata son wannan tafiyar sai don Yaya Habibu ya matsa mata. Amirun ne bata son gani, don bata son duk wani abu da zai taba zuciyar ta a halin yanzu. Ta riga ta sanyawa zuciyarta YAKANAH (sunan littafin Takori mai zuwa). Ta koya mata dangana, ta koya mata rayuwa ba AMIRU. Karatun ta kawai tasa a gaba, da rainon ‘ya’yan da Allah ya bata. Lokacin da Daddy ya gayawa Amiru mairo ta haihu har ‘ya’ya biyu, bai nuna wani farin-ciki ba, don yana kullace da Mairo, da bata taba zuwa ta dubashi ba har yayi ciwon sa da jinyarsa ya gama ya gaji ya mike. Bashi da wani sauran buri a rayuwa, tunda ya rasa Mairo. Sannan Daddy yace babu maganar biko, ba zancen kome, don bai yarda sun gama horuwa ba, Amirun yayi ta zama a gwauro, ko su aura masa mai haihuwa. Ya kuma ce da Amiru in zai mike ya fuskanci sabuwar rayuwa to ya mike, in bazai mike ba, yayi ta kwanciya soyayya ta kassara shi. Don shima yana da nasa laifin. Na kin gaya masa duk abinda ke faruwa saboda tsoro da son Hajiyarsa. Har saida komai ya lalace. Daddy yace “ita tana son ka ta lalata maka rayuwa?” A fannin ita Hajiya, zaman Amirun haka babu iyali ya fara damun ta. Tana so tayi zancen biko a maida aure tunda saki daya ne, babu fuska daga Habibu da Daddy. Don haka tasa ido, don ganin hukuncin da suke nufi. 8/9/21, 12:13 PM - Kawata: 33 Saidaifa rayuwar Amiru ta canza sosai. Ya zama babu murmushi babu far’a sai ‘dark-spaces’ kusan koyaushe make a fuskarsa. Sai ayyukan dake gabansa. Ya kudire a ransa idan ba Daddy ne da kansa ya bude baki yace ya maida Mairo ba da bakinsa, to ya hakura da ita har karshen rayuwarsa. Yamma lis, suka iso filin jirgin saman Abuja. Dina dasu Muhammad sukaje tareda direba filin jirgin suka dauko su. Suna zuwa gida Dina ta karbi yaran tayi musu wanka ta shiryasu da kaya na alfarma. Habibu ya dura su a mota tareda su Muhamnmad da mai rainon su Esta da suka taho da ita daga Malaysia sai Asokoro. Kasancewar ranar Lahadi ce, Daddy yana gida shida Amiru a karamin falonsa, suna aiki cikin takardu da kwamfuta. Habibu ya yi sallama rike da mai sunan sa yayinda Muhammad ya biyo bayansa dauke da Amir. Ya saki takardun hannunsa ya bisu da kallo. Ba zaka iya karantar halin da zuciyarshi ke ciki ba. Suka yiwa kansu mazauni a falon Esta tana waje, Daddy sai murmushi yake yayinda Amiru ya zamo mutummutumi, tsigar jikin shi na tashi cikin kauna da shauki. Ya matso ga Habib dake zaune a cinyar Habibu, ya durkusa a gabansa ya mika mishi hannu, siraran lebbansa dauke da wani irin ni’imtaccen murmushi, da bai taba yi a rayuwarsa ba. Wata irin kauna ta da da mahaifi ke fizgar zuciyar shi. Amma sai Habib ya noke a kafadar Yaya Habibu wato, bai san shi ba. Yaji ba dadi, ya koma ga Amir yana karkada mishi ‘ya’yan mukullai, da wayo da dabara ya samu ya yarda ya dauke shi. Ya rungumeshi sosai a kirjinshi yana sunsunar shi. Yana shakar kamshin turaren Mairo (Fahrenheit) daya kama jikin yaron. Ganin dan uwanshi a hannun shi sai shima Habib ya miko hannu, ya hadasu su duka biyun a kirjinsa, sai yaji kamar Mairo ce ya rungume. Amma don mazantaka, bai yarda ya zudda hawayen da suke son bashi kunya ba. Daddy da Habibu suka bisu da kallo cikin tausayi. Daddy yace “saukar yaushe?” Yace “dazunnan muka iso”. Dai-dai lokacinda Hajiya ta shigo falon cikin kwalliya ta alfarma. Bakinta ya fadada da far’a da murmushi. Tace “A’ah! Sababbin masu gidan sun zo, tsofaffi sai su zo su fice…” tana kallon Daddy tana dariya. Ya harareta don yasan dashi take, yace “da tsohuwar zuma ake magani. In dai wadannan ne da ba mazauna ba ai gaki gasu, da sun tafi zaki dawo min ne kina rara-gefe”. Ba yadda bata yi ba don ta dauke su amma sun like jikin Ubansu. Ta fita ta kawo ‘teddy’ na ‘ya’yan Nina da suka zo hutu sannan suka yarda da ita. Daddy yana son ya tambayi Habibu mai yasa Mairo bata zo ba? Yaga babu dalilin da zai yi masa wannan tambayar sai yayi shiru. Shikuwa Amiru Allah kadai yasan abinda ke cin zuciyar shi. Mairo ta daina son sa……! Mairo bata son ganin sa…..!! Har goma na dare suna can, yaran suka soma rigima, duk da an basu madara. Uwarsu suke so haikan. Amma Amiru ya kasa bada su. Saida Habibu yayi mishi alkawarin kafin su tafi gobe zai kai mishi su ofis sannan ya dauko su har motar Habibu, bayan Hajiya ta cika su da toshi. Daddy ma ya bada check na kudi masu yawa yace a dinka jamfa, baya son ganin su da daura ‘suit’ irinna Ubansu. Mairo tayi shirin barci a dakinta dake gidan Yaya Habibu. Ta sanya yaranta a gabanta tana kallon su da fuskar mahaifinsu. Tana sunsunar su da kamshin ‘miyaki’ wanda ya tuna mata da ‘those precious moments’ da suka shude a baya. Tana sunsunar su da kamshin ‘miyaki’ da suka kwaso, wanda ya dawo da so da kaunar mijinta sabo fil a zuciyar ta. Ta shiga tsakanin su ta rungume kowanne a jikinta. Ta soma sheshshekar kuka a hankali, na tashin tsohon mikin daya jima da samun sauki. Shiyasa bata so zuwa ba, amma Habibu ya takurata. Ta fadi a ranta Amiru ya daina son ta.......! Tunda har bai damu daya ganta ba. A karshe ta hakura ta sanyawa ranta salama. Tunda ance komai yayi farko, to inshallahu yana da karshe WATARANA! Washegari Habibu ya cika alkawari, ya sake diban Amir da Habib da Esta ya zuba su a mota zai fita da niyyar kaisu office din Amiru suyi sallama kamar yadda yayi alkawari. Yana kokarin tada mota Amiru na sanyo hancin motarsa ‘camero’ cikin get din Habibun. Don haka Habibun ya dakata har ya bude motar ya fito. Ya karbi ‘ya’yansa ya soma ‘kissing’ kamar bazai bari ba. Daga can saman bene Mairo ta yaye labulen dakinta don iska ta shigo. Nan ta hango su. Ta kurawa Amir ido. Bayan muguwar ramar da yayi, ya bar lallausar kasumba mara tsari ta cika fuskarshi, abinki da mai yawan gargasa. Sannan ya saya kwayar idon shi cikin ‘dark-spaces’ wanda ya hana mata gano halin da kwayar idanun shi ke ciki. Karan hancin ya kara fitowa, zirit, kamar karas. Wani irin so na fizgarta. Ta saki labulen a hankali ta koma da baya ta fada a gadonta. Tana mai fidda numfashi da sauri-da-sauri. INAMA ACE…….hannun agogo zai dawo baya??? *** Washegari suka koma Malaysia. Mairo ta fara karatunta cikin nasara, tana barin yaran a gida wurin mai rainonsu da yake an fara ba su madara. Kafin su cika watanni tara suna gudunsu ko'ina, musamman Alh. Abdurrahman ya bude mata 'account' a nan ‘Kuala-Lampur' duk wata yana sako mata makudan kudi na fita hankali, don lalurorinta da kula da ‘yan jikokinsa. Bayan kuma ba abin da Ambassada ya rage su da shi, ga na Yaya Habibu. Gaba da baya gata ya lullube Mairo da 'ya'yanta, abin sai godiyar Allah. Shekaru ukku cif, wadanda suka yi dai-dai da cikarta shekaru talatin a duniya, da kwalin digiri, master, da digiri na kololuwa. Dr. Maryam Muhammad Bedi, ta tattaro ta dawo gida Najeriya a garin Abuja, zuwa lokacin Habibu ya yi ficce, bankin ‘Habib Bank’ ya samu habaka zuwa 'branches' a dukkan 'thirty six states' da muke da su a gida Najeriya, kamar yadda Amiru Abdurrahman ya yi fata. Yau ga ci gaban ya samu, ba tare da Amiru ba. A wannan ranar da ake (ten-year anniversary) na cikar bankin shekaru goma da kafuwa, Habibu kuka yake, maimakon ya yi farin ciki. A yayin da al'ummar taron suka dauka kukan farin ciki yake yi, amma shi kadai yasan dalilin kukansa, wanda bai wuce na alhinin samuwar cigaban shikadai, ba tare da Amiru ba. A kalaminshi na karshe, bayan ya yiwa mahalarta taron godiya mara iyaka. Ya ce, "Ya tafi ya bar bankin da kewa, bayan shi ya kirkireshi. Ya bar bankin da babban gibin da har gobe bai cike ba. Na kuma tabbata har abada ba zai cike ba. Sakamakon dumbin ALHERINSA gare ni. A yau na tashi daga mamallakin ‘Habib Bank’, na kyautar da shi ga 'ya'yan AMEERU ABDURRAHMAN GAYA". Amiru ya daga ido yana kallon shi, extremely puzzled! To haka Alh. Abdurrahman. Ashe wannan shine kudurin da Habibu yace yana dashi kenan akan bankin, ya ki yarda amaida hannun jarin Amiru cikin bankin? Ya sanya hannu cikin takardu, lauyoyi suka diba, su ma suka rattaba hannu. Sannan ya ce, “as a servant, zan ci gaba da juya musu dukiyarsu har zuwa girmansu”. Hajiya ma ta dauko duk takardun dukiyar Amiru dake tare da ita, ta danka mishi. Ya hada dana wajen Habibu ya adana a bankin. A wannan ranar Habibu yayi kuka, kawai sabida tausayin AMEERU. Don gabadaya rayuwarshi ta canza ‘completely’ ta zama ‘no meaning…’ kamar yadda ya fadawa Mairo a baya. “My life has no meaning......idan ba tareda ke ba”. *** Habibu ya watsa mata takardun neman aiki, a manyan jami'o'inmu, tun daga Ile-Ife, Ahmadu Bello, Nsukka, Bayero, Lasu da sauransu, ba don neman kudi ba, sai don al'ummar Najeriya su amfana da ilimin da ta wanzar da rayuwarta tana nema, don su amfana. Ba da jimawa ba jami'o'i har biyar suka dauke ta, ciki kuwa har da jami'ar Abuja, wadanda ta bari a baya. Amma ta zabi BAYERO domin a ganinta al'ummar Kano su ne al'ummarta. Habibu bai takura mata da zancen aure ba, ko tayin ta koma gidan Amiru. Sai dai shima yana ganin lokacin yayi daya kamata a maidawa Amiru matarsa sabida yadda zawarawa manya-manyan kusoshi ke yi mishi rubdugu, a gida ne ko ofis. Alh. Abdurrahman ya fara tsawatar mata da cewa, ba zata koma Kano ba har sai ta fidda miji ta yi aure. Sai ta sa musu kuka tana rokonsu, kada su kara yi mata zancen aure, idan ba so suke ita ma CIWON ZUCIYAr ya kamata ba. Me zata yi da wani da namiji ba Amiru ba? Me zata nema a jikin wani namiji bayan Amiru? Amiru yasa ta raina sauran maza, ta yadda har basa burgeta, duk ilminsu da mukamin su kuwa. Gashi da alama Daddy baya son komen nasu. Tunda koda wasa bai taba furtawa ba. Ya kama Mairo da Habibu ya rungume kamar shi ya haife su, ya jibanci dukkan al’amuransu, amma baya ko son kallon Mairo da sunan matar Amiru. Itama kuma tunda hakane bazata taba nuna tana son komawar ba, koda hakan na nufin ta auri wani ne ba shi ba! Alh. Abdurrahman ya ce, "Aure ya zama dole Mairo, domin shi ne cikar kima, mutumci da darajar diya mace. Duka wadannan kwalayen naki aikin banza ne idan babu aure". Ta yi masa alkawarin su barta ta fara aikinta, a hankali za ta zabi wanda hankalinta ya kwanta da shi. Ya so ya karbe yaran, amma ta roke shi ya bar mata, zuwa wani dan lokaci kalilan, don suna debe mata kewa. Gida guda suka bata cikin 'new site', suka tare ita da 'ya'yanta da mai rainonsu, mai suna Lami. A lokacin Lawan da Ahmad 'ya'yan Baffa suna karatu a Bayeron, sai suma suka dawo gidan suna zaune a baskwata. Baffa yana zuwa duba su akai-akai, su ma suna zuwa idan sun sami lokaci. Mairo ta fara 'lecturing' a 'department of sociology' cikin nasara da sanin makamar aiki. Ta sanya yaranta a 'staff-school' kullum su Lawan suna kaisu su dauko su, da yamma kuma su kaisu islamiyya da ke nan cikin 'New-site'. Ta dade da fara rubuce-rubuce tun tana Malaya akan fannin da ta ke karantarwa, wanda ya kaita ga matakin zama 'proffessor' cikin dan lokaci kalilan. Kyawunta, zurfin iliminta, sakin fuskarta da yawan taimakonta ga dalibanta, ya sanya ta zamo abar so ga dalibanta. Sai dai fa kowa yana bin kwakkwafi ya yi mamaki idan aka ce ba ta da aure. Sukan ce kyakkyawar mace kamar wannan ace ba ta da aure, ai abin mamaki ne sosai. Sannan kallo daya zaka yi mata ka tabbatar ba da wannan aikin ta ke cin abinci ba. Tana dai yi ne don ra'ayi, amma ba don neman wani abu wai shi 'kudi' ba. Proffessor Maryam Muhammad Bedi, ta zamo daya daga cikin malaman da ake ji da su a jami'ar Bayero, ko sabida karyayyen harshenta na Turawan America zallah. Don haka da yawa suke bin kwakkwafi akan rayuwarta, har su san inda ta samo wannan 'background' din. Wani dalibinta ya soma rubutu a kanta, sai dai duk yadda ya so ya ji tana da aure ko ba ta da shi, ba ta bada wannan damar ba. Dr. Mairo ta shiryawa dalibanta masu fita a wannan shekarar 'conference' mai taken, “YADDA ZA A GYARA AL'ADA TA YI DAI-DAI DA ADDINI” Wanda take so Mai girma sabon V.C ya halarta. Don haka ta je ta nemi 'appointment' na ganin V.C a ofishinsa. Aka sanya ta cikin jerin wadanda za su ga V.C a safiyar washegari. Da ta dawo gida ta tarar Lawan ya dawo da su Habib, Amir yana kwance shiru cikin kujera ba kamar yadda ya ke ba. Ta dora hannu a kanshi, zafi rau, Lawan ya ce. "Amir ba ya jin dadi tunda safe". Ta ce "Za mu je asibiti da safe, idan na ba shi 'paracetamol' zazzabin bai sauka ba". Ta dauko 'paracetamol' cikin 'first-aid box' dinta ta ba shi da dan kankanin cokali. Har zuwa washegari zazzabin bai sauka ba. Ga shi kuma tana da 'appointment' na ganin V.C, don haka ta sa yaran a bayan mota suka nufi cikin makaranta da zummar idan ta ga V.C sai ta wuce da su asibiti, don mawuyaci ne daya ya yi ciwo dan uwansa bai kama ba. Ba ta barsu a mota ba, sanya su ta yi a gaba suka soma taka matattakala wadda zata sada su da ofishin V.C. Mutum biyu ne a gabanta, sai da ta jira suka fito, sannan ta kama hannun Habib da Amir suka sanya kai cikin ofishin, bakinta yana mai furta sassanyar sallama. Ya juya baya yana zakulo wasu takardu cikin loka. Idanunshi saye cikin farin gilashi, sanye cikin farar shadda 'excelsior' dinkin Muhammed Abacha. Hular kanshi na aje bisa teburinshi. Gaban Mairo ya yi wani irin mugun faduwa, takardun da ke hannunta suka kwace suka watse a kasa. Amir ya tsugunna yana tsince mata. Shi kuwa Habib tattakawa yakeyi da cambos dinsa. Ko mutuwa ta yi ta dawo, ba zata mance surar UNCLE JUNAID ba, wanda ke tsaye nan a gabanta. Sai dai wannan Junaidun, ya sha ban-ban da wanda ta sani shekaru goma sha biyu a baya. Wannan cikakken magidanci ne, da yasha gwagwarmayar rayuwar neman ilmi cikin fanninnika daban-daban, ba dan saurayi Junaid Galadanci ba. Duk da alamun shekaru da suka hau kansa, har yanzu yana nan a Junaidunsa da ta sani, ma'abocin zati da kamala, gami da kwarjini bayyananne daga Sarkin halitta. Ta rasa cikin halin da ta samu kanta, rudewa ce ko gigicewa ce? A'a, ko kuwa gaba daya makuwa zata ce ta yi? Ta juya da baya–da-baya zata bar ofishin, ya juyo a hankali ya dubi mai shigowa. "Mariama!" Maironshi da a kullum ta ke zuwa a farke, ko cikin mafarkinshi. Mairon da dai-dai da rana daya cikin shekaru goma sha shidda, zuciya ba ta taba hutawa da kaunarta ba. Ruhi bai bar mafarkinta ba, haka tunani bai taba kuskuren manta ta ba. Ya dago Habib ya dauke shi tare da kama hannun Amir ya zauna a kujerar da mutane suke zama don ganawa da shi. Cikin wata irin kassararriyar murya, ya ce. "Ya ya za ki koma? Ko ba ke ce 'Proffessor Maryam Bedin ba?" Ta ja tunga a jikin kofa, ba tare da ta juyo ba. Ita bata fita ba, ita bata juyo ba. Hannunta jikin marikin kofa, ta ce "Ni ce". Ya ce "To mene ne ajandar?" Ta ce "Na zo neman alfarmar V.C ya samu halartar 'conference' dina ne". Ya yi murmushi yana dauke da Amir ya tako har inda ta ke tsaye. Wani irin sassanyan kamshi da ba zata ce ko na wanne turare ne ba a duk iya sanin da ta yi wa turare ya kassara mata gabbai. "Na kasance ma'abocin son 'twins' Dr. Mairo, ko za ki bani aronsu? Na dawo miki da su bayan awanni goma sha biyu?" Wannan karon ne ta juyo ta dube shi, wasu kibbau na tsohuwar soyayya suka soki idanun kowannensu. Tsohon tsimi ya tashi, wanda ya yi sanadin tashin tsigogin jikin kowannensu. Da kyar ba tare da ta sake yarda sun hada ido ba, ta ce. "Idan iyalinka suka tambaye ka ina ka samo su mai girma V.C me zaka ce musu?" Babu bata lokaci, ya ce da ita. "Ya'yana ne, wadanda Mairon Gurin-Gawa ta haifa mini..............." Kuka ya kece mata, don haka da gudu ta fice daga ofishin tana ji a ranta, ta fasa yin 'conference' din, tunda shi ne ya yi sanadin da ya taso da tsohon gyambon da ya dade da warkewa a zuciyarta. Gidan Baffa ta wuce kai tsaye, ta nufi dakin Habiba ta kwanta tana sakin ajiyar zuciya mai nauyi. Ta yi juyi a lallausan gadon Habiba tana tariyo abinda ya faru cikin 'yan mintina kalilan. Baffa ya shigo dakin ya zauna a kujera yana fuskantarta, ta goge hawayenta, ya ce. "Me ya faru? Ke dai har gobe abun kuka ba shi da wuya a wurinki? Yanzun nan Habiba ta yi min waya ta ce, kin shigo da gudu kina kuka. Idan ka girma sai kasan ka girma, ka koyi dauriya da juriya irin ta manya. Ba akan kowanne kankanin abu ka bare baki ka yi ta kuka a gaban mutane ba". Ta yi murmushi tana goge hawayen idanunta, ta ce. "Baffa, Uncle Junaidu na gani, bayan wucewar shekaru goma sha biyu. Ya tuna min da abubuwa da dama da suka faru cikin rayuwata, shine dalilin kukana, domin na tuna abubuwa da dama da yanayin shekaru da cigaban rayuwa ba su sani na manta ba". Ya ce, "kwanannan naji a labarai anyi ‘appointing’ din shi matsayin shugaban jami'ar Bayero ai. Har yau har gobe kuma bai fasa zuwa gidan nan yana gaishe ni ba, bai fasa yi min manya-manyan alhairori ba. Sannan son ki har yau bai barshi ba. Ban taba ganin 'SOYAYYAH' irin ta Junaidu ba. Don haka ni ma har gobe ban fasa yi mishi addu'ar budi da nasarar rayuwa ba". Mairo ta cika da mamakin jin cewa Uncle Junaidu na zuwa wajen Baffa har yau. Amma koda wasa Baffan bai taba gaya mata ba. Ba ta gama mamakinta ba su Habib suka shigo suna ta tsalle, kowannensu rike da kit-kit da leda fal 'choculates' suka fada jikinta. "Mummy mun dawo... Daddy yana gaishe ki". Sai Baffa ya tashi ya fita, ya tarbi Junaid a dakin bakinshi. Habiba ta shigo dauke da kulolin abinci. Su Amir suka makale ta suna ta ba ta labarin inda Daddy ya kai su. Ta ce, "Wai wane ne wannan Daddyn?" Amir ya ce "Daddyn Mummy ne". Mairo ta ce "Rabu da shirmen su Mama, shugaban jami'armu ne". Habiba ta yi murmushi ta ce. "To ko da shi za a yi ne?" Ta yi shiru ta daure fuska bata bata amsa ba. Don ba abin da ta tsana a rayuwarta irin a yi mata zancen aure. Baffa ya dawo dakin yana murmushi, ya same ta tana cin abinci. "Idan kin kare sai ki je ku gaisa da Alhaji Junaidun. Daga nan ya ce yana so zai kai Amir asibiti, don ya ga alamun ba shi da lafiya". Matsayin Uncle Junaidun da kimarshi da ke zuciyarta, ya fi gaban ta ce ba zata je ba. Baffa ya ci gaba da yi mata nasiha mai sanyaya zuciya da sanya imani, akan lokaci ya yi da ya kamata ta tsaida hankalinta wuri guda ta yi aure, domin cikar mutuncinta a duniya da lahira. Tunda Amiru da Daddynshi basa bukatar komen. Ta yi sallama a kofar dakin, yana zaune cikin kujerun (leather) da suka yi wa dakin kawanya, Habib da Amir akan cinyoyinsa, yana ta haba-haba da su kamar ya maishe su cikinsa. Ya dago idanunshi da suka yi fari sol, yana dubanta. A zahiri Maironshi ce, sai dai fa wannan Mairon babbar mace ce 'yar shekaru talatin da doriya, wadda kuma a idanunka da kiyasinka ba zata fi shekaru ashirin da biyar ba. Wannan bakauyar da aka kawo mishi kafafuwanta jawur cikin lalle tsohuwa ta fada kwata, fatar kamar shuni, yau idan ka dube ta, tsammani zaka yi Balarabiyar Omman ce, ba wai 'yar asalin kauyen Gurin-Gawa ba. Kallonta ya ke, kallon da ke nufin al'amura da dama. Ita ma kallonshi ta ke, kallon da ke tuna mata da al'amura da dama. Da gaske Uncle Junaidunta ne, sai dai wannan ya kara yi mata GiRMA. Ta TUNA BAYA... ta tuno ALHERInsa gare ta, ta tuno SIRADIN RAYUWArta, ta yi ALKAWARI ko BAYAN RANTA matsayinshi ba zai taba canjawa daga zuciyarta ba. Cikin muryar GIRMA ya ce. "Mairo, ina Amiru Abdurrahman?” Ta kai gefen mayafin abayarta ta dauke wasu siraran hawaye da suka kawo mata zarya. A hankali tace. “Mun rabu!” Duk suka yi shiru na 'yan dakikai. Can kuma ta kawar da shirun da cewa. "How comes kai ne sabon V.C dinmu, amma ban taba sani ba?" Shi ma ya yi murmushi ya ce. "Ni nasan kina cikin 'proffessors' saidai ban tabbatar ba, sannan ban taba tunanin ba kya tare da maigidanki ba, a wane dalili zan nemeki? Sannan bani da tabbacin ke din ce ko ‘namesake’ dinki ce, na dai ga sunan da ya tsayamin arai ‘among the proffessors’, Sannan ai ban dade ba ai, banyi dadewar da zaki san ina cikin makarantar ba” tace “haka ne”. Ta sunkuyar da kai kafin ta dago ta sake cewa "Ikon Allah kawai". "Ni ma sai ki dauke shi a hakan, wato kudurar Allah, ta fi ga haka". Ta jinjina kai, ta ce "Kwarai kuwa". Suka maida idanunsu akan Habib da Amir, wadanda ke ta dabdalarsu cikin dakin, dukkaninsu sai suka yi murmushi, yaran suka burge su. "Kuruciyarsu na da ban sha'awa". Ya fada a zuci, bai san cewa a fili yake fadi ba. "Kamar kuruciyar Mairo, Mairon Baba da Inna, Mairon Kausar da Nabilah…….." Ta yi dariya ta juyar da kanta. Wani ala’amari mai girma na cin zuciyarta. Sai dai ba irin wanda take ji a tsohon mijin ta ba. Ya kura mata ido, zuciyarshi na harbawa. "Ina labarin Nabilah da Yaya Habibu?" "Nabilah tana nan Kano, 'ya'yanta biyar. Yaya Habibu yana Abuja". "Nima na yi aure Mairo. A lokacinda na riga na sallamawa zuciyata cewa na rasa ki, bazan same ki ba, kin riga kin yimin nisa, kin zama matar wani na. Wanin da nake da tabbacin ko mutuwa yayi bazai tafi ba tareda igiyoyin aurenki ba. A halin yanzu Ina da 'ya'ya biyu, tareda ‘yar uwata Ikhlas. Sai dai har wannan lokacin da tunanin Mairo nake kwana nake tashi. Sannan dashi nake ‘functioning, will you believe it?” Ta dago fararen idanunta ta haske shi da su. Tace “sabida me Uncle?” Babu jinkiri, babu inda-inda ya rausayar da kai ya ce "sabida Soyayyarki Mairo! Soyayyar da na ke yi miki a wancan lokacin Mairo, ta zarta hankali, ta zarta duk wani kokarin hankali na ya fassarata. Mahaukaciyar soyayya ce Mairo, wadda ta makantar da ni daga daga ido na dubi sauran mata. Ta dakusar da hasken mata ta Ikhlas daga cikin idanuna. Na tabbatar tunda na rasa Mairo, to bazan samu makwafinta ba. Don haka ne Hajiya tasha wuya da fari kamin inyi aure. Don nasan ko na yi, to bazan baiwa matar hakkokin da addini ya ce na ba ta ba. Ba zan iya sallama mata zuciya da gangar jikina ba". Ya taso ya tsugunna a gabanta, yana so su hada ido, amma ta ki hakan. Ya dora hannunshi akan tafin kafarta. Ta lumshe ido a hankali ta bude su akan yatsun hannunshi da ke bisa tafin kafarta. Ya dauke hannunshi ya zauna sosai a gabanta, ya ci gaba da cewa. "Hajiyata ta shiga tashin hankali mai yawa, ta yi kuka, ta yi rokon duniya akan na yi aure, na kasa Mairo. Daga baya sai malamai ta sa suke yi min rokon Allah, sun tabbatar mata da zan yi aure, sai dai da sauran LOKACI, tunda zuwa yake. Daga baya sai ta koma nasiha, amma zuciyata ta riga ta bushe. Na tabbatar mata idan dai ba so ta ke na auri matar na dinga daukan alhakinta ba, to ta kyale ni. Haka ta hakura ta zuba min ido, amma ta ce ba ta fasa yi min addu'a ba. A yau ina da yakinin Allah Ya amsa addu'arta. For the first time da na ke ji a jikina LOKACI ya zo da zan yi AURE ba irin na Ikhlas da ya zamto hadin iyayen mu ba. Wanda akayi ba tareda anyi shawara dani ko neman yarda ta ba. 8/9/21, 12:19 PM - Kawata: 66 khlas diyar kanin mahaifina ce da Hajiya ta nema min aure bayan na kammala phD dina. A yanzu haka muna da Maryam (namesake) dinki da Sabir. Yau ne na ji wani 'feeling' a zuciya ta mai tuna min da cewa nima namiji ne KAMAR SAURAN MAZA. Wadanda ke da buri a rayuwa, da kuma ‘hope’ (fatan) cikar burin nasu. Shin za ki tallafe ni Mairo? Ki auri tsoho in his fourteeth?" Hawaye na gudu a kundukukinta, ta ce. "Uncle Junaidu idan ka kira kanka 'tsoho' ni kuma na kira kaina me? Tsohuwa?? (second hand)? Ka bazawara...???" Ya yi saurin kai hannu ya toshe mata baki ba tareda yayi niyyar hakan ba. Da sauri kuma ya dauke hannunsa... "Ni har gobe a Maironki na sanki, koda kuwa ace ke kika haife B.U.K baki dayanta…..." "Idan haka ne, ni ma har gobe a Uncle Junaidu na sanka, bana son kara jin wannan kalmar ta fito daga bakinka 'tsoho’. Ya yi murmushi, ya ce. "Da dai ana sakewa tuwo suna ne Mairo..." Ta ce "Ni ma ban ce a sake masa ba, a barshi a tuwonsa, don haka zauna a Uncle Junaidunka ba V.C Junaid ba, na zauna a Mairona…....". Suka bi junansu da kallo, kallon yarda, so da kauna da aminci. Gaskiyar masu iya magana da suka ce, 'Soyayya ba ta tsufa, sai dai msoyan su tsufa’. Don haka sai mu bi JUNAID da MAIRO da fatan ALHERI. *** Alhaji Abdurarhaman ne ke zarya tsakanin falonshi da falon Haj. Aisha yana duba agogon hannunshi, yana kuma azalzalarta kan ta yi sauri ta shirya jirgi ya kusa tashi, wanda zai tashi dasu zuwa Kano a sanyin safiyar ta ranar litinin. Amiru baya nan ya je China, don shigo da wasu kwanfutoci sabon shigowa, Zuwa wannan lokacin ya yarda da nadamar ‘ya’yan nasa, da cikar YAKANAH da jarumtakar Amiru. Shekaru uku kenan da rabuwar shi da Mairo ba tare da ya kara sanya ta a idanunshi ba. Ya tattara karfin zuciyarshi ya karbi rayuwa ba Mairo, yana ganin lokaci ya yi da ya kamata yai surprising din sa, da abin da zuciyarshi ke ciwo dominta. Da abinda rayuwarshi ke muradi......... Duk wasu experiments.......... da ya dora shi a kansu...... bai fadi ko daya ba!!!. Sannan Mairo ta kammala karatunta cikin kwanciyar hankali, duk wasu burirrikan rayuwarta ta cika su, kamar yadda dan uwanta ke so. Ya kira Habibu a waya ya ce su hadu a Kanon gidan Baffa suma za su taho yanzu. Amina ta fito daga daki cikin shiri itama ta ce, “Daddy don Allah zan biku Kanon, ina son ganin Amir da Habib”. Ya ce “Wuce muje Amina ‘yar albarka”. (Amina mijinta ya rasu ne, a yanzu haka zaune take a gida). Hajiya ta fito cikin shirinta, suka nufi cikin chevrolet din Daddy zuwa filin jirgi, inda suka tarar jirgin ya kusa cika, don haka suna shiga ana rufe jirgin. Ba da jimawa ba ya soma keta hazo ya lula cikin sararin samaniya. Suna isa Airport din Malam Aminu, suka tarar da Habibu ya riga su isowa, ya kwashe su zuwa Yakasai gidan Baffa. Daidai lokacin da Mairo ta yowa Uncle Junaid rakiya zai tafi, tana dauke da Amir yana dauke da Habib. A kuma daidai lokacin da Habibu ya sanyo hancin motarsa wadda ke dauke da su Daddy harabar gidan. Daga Habibu, Daddy, Hajiya da Amina babu wanda zuciyarshi ba ta buga ba da ganin Mairo da wannan sankacecen mutum, ma’abocin zati da kamala, da kwarjini bayananne daga sarkin halitta. Karo na farko da Uncle Junaid ya dora idonshi a kan Yaya Habibu da baya bukatar a gabatar mishi, sakamakon tangamemen hotonsa dake sitting room din Baffa. Shima Habibu a take ya gane wannan shi ne JUNAIDUN MAIRO, da Baffa ya kyankyasa mishi a waya, cewa ya dawo neman auren Mairo. Jikin Habib a sanyaye ya fito daga motar, gwiwoyinshi kamar an rarrade su da murfin kwano. Suka yi hannu da Uncle ya yin da Uncle ya kai gwiwoyinshi kasa yana gaida Alh. Abdurrahaman. Amina ta mika hannu ta karbi Amir a hannunshi suka hada ido da Junaidun. A take ya ga fuskar Amir da Habib a fuskarta, ita kuma ta ji wani ‘magnet’ na jan zuciyarta a kan wannan mutum da ba ta sani ba, ba ta taba gani ba. Ya dago suka hada ido ta yi saurin sunkuyar da kanta. Mairo na son gabatar da Yaya Habibu ga Uncle amma kunyar su Daddy ta hana ta. Ya shiga mota ya tafi su Amir na ta kuka sai sun bishi. Hajiya ta kama hannun Mairo, Amina kuwa rungume ta tayi tana hawaye, a haka suka shiga dakin Habiba. Shi kuma Habibu da Daddy suka wuce falon bakin Baffa. Cikin dan lokaci Habiba da Hajara sun baibaye su Hajiya da cima ta girmamawa da ruwa da lemu, sun zauna ana ta gaggaisawa. Mairo da Amina dakin Hajara suka wuce suka bar Hajiya da su Habiba. A nan ne Amina take labartawa Mairo rasuwar Ghali (mijinta) watanni biyar da suka gabata. Ba tare da Allah ya basu haihuwa ba. Mairo har da hawaye na tausayawa Amina, don ita kanta shaida ce a kan matsananciyar soyayyar da suke yiwa juna. Mairo na so ta tambaye ta AMEERU ba ta so ta bada kanta. Amiru ya yi mata miki mai girma a zuciyarta. Tunda suka rabu bai taba nema ko sau daya ya ganta ba, sai ‘ya’yansa. To akan me ita zata nemeshi? Ta tabbata duk inda yake yanzu ya dade da shafe ta a babin rayuwarsa. Watakila ma ya kara aure bayan Hanan, ya sallamawa wata wannan gangar jikin da ada ta dauka mallakinta ne ita kadai. Don ta san Dan Abdurrahaman Gaya, ba zai iya kaiwa tsawon wannan lokacin ba tare da aure ba, in ta yi la’kari da halittarsa, na mutum mai tsananin yawan bukata. Sannan Hanan, bata da surar irin matar da yake son aure. Ko kuma watakila ya komawa banasariyar matarshi? Allah masani. Amina ta ce “Rayuwa tafe take tare da destiny (kaddara) kala-kala Aunty Mairo, kin manta da brother, kin bude sabuwar rayuwar da ta bani mamaki, kin kara kyau, kin kara kiba, kin kara haiba da kamala. Sabanin shi da a kullum yake kara lalacewa. Cikin shekaru ukun nan ban kara ganin dariyar Yaya Amiru ba, ki yafewa mai kaunarki wanda ya sadaukar da zuciyarsa ga soyayyarki. Ku tallafi juna, ku baiwa zuciyoyinku abin da suke so. Hajiyata da ‘yan uwana sun yi kuskure, sun kuma gane kuskuren su, sun yi nadama mai suna nadama amma ku, (keda Amiru), Daddy da Habibu har yau kun ki karbar tuban su, ban san me yasa ba”. Mairo ta yi murmushi wanda iyakacinsa fatar bakinta, ta ce, “Mun karbi tubansu man? Watakila dai iyakar zaman ke nan, babu saura, tunda aka kawo wannan lokacin. Shi ya gaya miki yana son komen? Yana da mace irin Hanan a gefe?” Mamaki ya kama Amina, ta tabbata Mairo ba ta san tare suka yi waje ita da Hanan ba. Ta ce, “A kan sakin Hanan aka yi naki, Allah sarki brother! Zurfin cikin shi na bani mamaki. A halin yanzu Hanan tana Porthercourt ‘ya’yanta biyu tare da mijinta Ramadan wani ma’aikacin kwastom”. Mairo ta yi shiru, kamar an zuke jinin jikinta. Tausayin Amiru ya kama ta, Allah kadai ya san halin da rayuwarshi ke ciki. Ta tura hannu cikin jakarta ta zaro wasu kananun katina da aka yiwa rubutu da kumfar golden, ta dorawa Amina a cinya. A kasalance Amina ta dauka, kati ne na gayyatar daurin auren PROF. JUNAID ATIKU GALADANCHI da DR. MARYAM MOHAMMAD BEDI, wanda za a gabatar kwanaki goma sha hudu masu zuwa. Ba ta kai karshen karanta katin bikin ba Amina ta rushe da kuka. Ashe masu kukan suna da yawa, domin a can falon Baffa ma Hajiya ce ke ta kuka tana rokon Alh. Abbas ya yi wa Amiru uziri, su ne da laifi ba shi ba. Su kuma ba su yi hakan da nufin A BARI YA HUCE...... ba, sai don a bawa Mairo dama ta sarara ta cika burin neman iliminta. Cikin nutsuwa da kwanciyar hankali Daddy ya ce. “Idan da mai laifi to ni ne, don ni na hana Amiru yin wani yunkuri na dawo da iyalinsa har tsawon wannan lokacin. Ina so in koya masa jarumtaka, in nusar da shi cewa; “kallafa rai a kan abin da ake so, da amanna da cewa samuwar abin nan kadai shi ne samun lafiya da kwanciyar hankali ba shi ne ba”. Dauriya, hakuri da juriya da tawakkkali sune halayen da ake son namiji ya suffantu dasu. Kuma na gode Allah....... DUK WASU EXPERIMENTS DANA YIWA AMEERU BAI FADI KO DAYA BA..............!!!” Baffa ya jinjina kai ya ce. “Nima in son samu ne, na fi son Mairo ta koma wurin mijinta ta tarbiyanci ‘ya’yanta a gabanta. Amma Alh. Junaidu ya zarta duk yadda kuke tunani a wurin mu. Don haka bana cikin wannan magana..... Zabi yana ga Mairo, tunda ita Allah ya baiwa damar zaben mijin da za ta iya zama da shi a halin yanzu. Don haka ku bani kwana biyu zan tuntube ta”. Habibu bai ce komai ba, don ba shi da ta cewar, bai san me zai ce ba, bayan Allah ya yiwa Mairo zabin alheri, wannan karon ba zai yi shisshigi ba. *** SUNA tafe cikin jirgi amma Daddy baya cikin nutsuwa. Tausayin gudan ransa ya ishe shi, ko ma me ya faru ya tabbata shi ya jawo mishi. Shekaru uku ba kwana uku ba!!! Ya nesanta Amir da iyalinshi a kan laifin da ba nashi ba. A kan hujjojin sa da basu da karfi. Don haka suna sauka a jirgi ya bude waya ya kira Amiru yana nishi kamar mai ciwon asthma. Ya ce, “Ka bar duk abin da kake ka taho, ka wuce Kano ka nemi sasanci da iyalinka in har kana so. Na amince maka Amiru, da sanya albarkata.... saura kwana goma sha hudu a daurawa Mairo aure!!!” Ga mamakin Daddy sai ya yi murmushi, wanda har sautinsa ya ratso cikin wayar, ya ce. “Ka kwantar da hankalinka Daddy, na dade da sanyawa zuciyata salama, na yi amanna da cewa idan akwai sauran zama tsakanina da Mairo, to za ta dawo mini ko ba dade ko ba jima”. **** Lawan da Ahmad ‘ya’yan Baffa ne a harabar gidan Dr. Mairo, wanda ke a Area C cikin sabuwar jami’ar Bayero suna wasan kwallon kwando, ya yin da a gefensu Habib da Amir ne tare da wasu sa’o’insu ‘ya’yan makota suke wasan tsaren kekuna, yara masu ban sha’awa. Suna sanye da kayan sanyi masu laushi farare sol, an rubuta I LUV MUMMY, kafafunsu daure cikin farin cambas, sunyi kyau har sun gaji kamar ‘ya’yan South-Western. Daidai lokacin da motar kirar (Camero, 2 Door) ta yi parking and hankali a gefensu, matukin motar ya duba katin da ke hannunsa ya tabbatar lambar gidan ta yi daidai da wadda ya gani a rubuce. Sai ya kashe ya fito. Sanye yake da suwaitar ‘Dolce & Gabbana’ mai dogon hannu, da shudin wandon jeans. Ya yin da rigar ta kasance fari da ratshin ja da blue. Ga duk wanda ya san shi, ba zai yi gaggawar gane shi ba, saboda yadda fatar jikinshi ta kara kwanciya, tare da goguwa mai nuni da alamun hutu. Ya jawo bakin PRADA ya saya kwayar idanun shi. Daidai lokacin da idanunshi suka kai ga sanyin idaniyarshi. Ya dade yana kallon su yana murmushi, har bai san tsayin mintunan da ya bata a tsaye ba, ba tare da yaje gare su ba, don ganin yadda hankalinsu ya raja’a a kan wasansu. Har sai lokacin da Amir ya karawa Habib keken shi ya fadi, ya sanya kuka. Da sassarfa ya karasa garesu, ya mika hannuwa ya dauki Habib wanda ke ta kuka ya rungume a kirjinshi, ya kuma kama hannun Amir suka doshi kofar gidan. Su Lawan suka gaishe shi suka koma ga kwallon su, Lawan na radawa Ahmed Baban su Amir ne. Aikin marking takardun dalibai ya kacame mata, ta yi dai-dai da takardu a tsakiyar falon sanye cikin riga da wandon da basu kama jikinta ba, kanta babu kallabi, tufkar gashinta a tsakiyar kanta. Fatar nan ta kara zama fresh ta nuna mace danya sharaf, mai wadatar jini a jika, ta yadda ba za ka yi tunanin ta taba haihuwa ba. Sassanyan kamshin ‘miyaki’ da ta dade da sani ne ya bakunci hancinta. A razane ta cira kai. Ta sake yin arba, da dan Abdurrahaman Gaya. Rungume da ‘yan biyunshi masu tsananin kama dashi. Sai dai wannan AMIRUN ya sha banban da wanda ta bari shekaru uku a baya. Ya sirance, ya bar lallausar kasumba ta bata kyawun shi da tsarin shi, duk da haka yana nan a Amirun sa, dan gaye, mai kyau, kuma mai sanyi, wanda idaniya ba za ta taba gajiyawa da kallon shi ba. Mikewa ta yi tsaye kamar an umarce ta da yin hakan, alama ce ta girmamawa a wajen bature. Ta rasa cikin yanayin da ta tsinci kanta tsakanin rudewa da gigicewa. Sannan wani sanyi ya tsirga a zuciyarta, ta lumshe ido ta bude, ta tabbatar shi din ne, ba mai kama da shi ba. Kafin ta yi wani action ya daga dogayen kafafunshi da sassarfa ya isa gareta, ya hada ta ita da yaran ya rungume, jikinshi in ban da kyarma ba abinda yake. Ya kankame ta ita da yaran hawayenshi na sauka a gadon bayansu. Ya ce, “Mairo kin yi min alkawari........ ba za ki taba barina ba, kin yi min alkawari...... we are meant for each other. Me yasa kika karya? Kin riga kin sani kowanne numfashina yana fita ne tare da sunanki. Me yasa kika amsawa Uncle Junaidu, kika kasa jirana mu maida auren mu? Kika kasa yi min uziri? Uzurin da zan yiwa Daddy biyayya, kada ya ga rashin juriyata? Ya ya zamu yi da ’ya’yan da Allah ya bamu bayan fidda rai da samun su? Baki yi sha’awar ki rayu tare da su ba? Ki basu tarbiyya irin taki? Jarrabawa ce Allah ya yi mana, kuma mun cinye ta da ikonsa, yanzu ne ya kamata mu karbi sakamakon mu. Zan nemi Uncle Junaid in roke shi alfarmar ya bar min ke, ko da hakan na nufin zan durkusa masa akan gwiwoyina, don na fishi bukatarki, ‘ya’yanmu sun fishi bukatarki. Kalle ni. Am all alone Mairo, leading a shattered life.........!!! Dukkansu basu ankara da wanzuwar mutum a falon ba, tsayin lokacin da suke rungume da juna suna kuka dukkaninsu, su suna yi ‘ya’yan na yi. Sai jin karar rufe kofa da aka yi a hankali, suka juyo dukkanninsu, babu kowa! Amma kamshin ‘Irresistible Givenchy’ da Mairo ta ji, ya tabbatar mata da ko wane ne ya shigo, ya kuma fita, ba tare da ya yi wani motsi da zai katse su daga kololuwar duniyar shaukin soyayyar juna da kewar juna da suka fada ciki ba. Hankalin Mairo ya tashi, ta tabbatar Uncle Junaidu ya ga Amiru, cikin halin da ita kanta ba ta san wanne ne ba. Ta zame da karfi, da gudu ta biyo bayan shi amma sai kurar motarshi da hasken fitilar motar shi ta gani. Ta rasa ina za ta sa kanta, sai ta kifa kai cikin tafukanta ta soma kuka. La shakka maza biyu take so, ba ta san ya ya za ta yi dasu ba. Lallashi na duniya, ban baki na duniya Amiru ya yi amma Mairo ta ki ce da shi komai. Ransa ya fara baci, amma ya danne fushinsa, tunda mai nema.....baya fushi. Ya ce, “Shi ke nan na tafi Mairo, na ba ki daga yau zuwa gobe ki yi tunani, zan je wajen Baffa daga nan zan wuce inda na yi masauki, sai gobe insha Allahu”. Ya dauki Amir ya kama hannun Habib za su fita, ta taso da gudu ta rike rigar shi ta baya cikin kuka ta ce, “Ina za ka kai su?” Ya harare ta ya ce, “Gidan ubansu, tunda bakya son ubansu to suma bakya son su”. Ta ce, “Ni na ce hakan?” Ya yi mata kallon rahma, sannan ya ce, “Za su taya ni kwana ne”. Ba ta yi magana ba, ta shige daki ta hado musu duk abin da za su bukata cikin karamar jaka ta ba shi. Suka ce, “Mummy bye-bye”. Ita ma ta daga hannun tana yi musu bye-bye din har suka fice daga falon. Cikin hanzari ta dauki waya ta soma kiran nambar V.C Junaidu, bugu daya ya amsa, babu komi cikin muryarshi sai kulawa ya ce, “Ya aka yi MARYAMA?” Ta shafe hawaye ta ce, “Ka fasa zuwa yin ‘dinner’ din?” Ya yi murmushi ya runtse idonsa, tsigar jikinsa na wani irin tashi saboda KISHI. Idanunshi na tariyo mishi hoton abin da ya gani, wani image da bai taba ganin mafi muninsa a rayuwarsa ba, cikin sanyin murya ya ce, “Na zo na tarar kina da bako, don haka na tafi”. A raunane ta ce, “Ba bako bane Baban su Amir ne ya zo ganin su”. A ranshi ya ce, “Ka ji rainin hankali irin na ‘ya’ya mata....”. Amma a zahiri ya ce, “Ki saurare ni, idan na gama da Baffa zan kira ki”. Ya kashe layin. Damuwar duniya ta ishe ta, ta kuma rasa abin yi, ta shiga halin rudani. Wadannan dakarun maza, jaruman soyayya sun sanya ta a kwana. Tana neman Dina, tana neman Nabilah..... don neman shawara, tunda an ce “Aikin mai shawara baya baci”. Ta kira wayar Nabila, ta ce, “In kina gari zan zo gobe around 11”. Ta ce, “Ina nan amaryar uncle sai kin zo”. 8/9/21, 9:04 PM - Kawata: 87 Junaid na yin parking a harabar gidan Baffa, shima Amiru na sawo kai, suka yiwa juna kallon-kallo, bayan kowanne ya fito daga motarsa. Kwayar idon Amiru har girgiza take saboda KISHI, akwai wani feeling na kishi iri daya a zuciyar kowannen su, sai dai babu wanda ya bari nashi ya fito fili. Da sauri Amir da dan uwansa suka balle kofa suka nufi Uncle Junaid suka rungume kafafun shi, ya russuna ya kama kowannen su da hannu daya ya dauke su, suna ta zuba mishi surutu wai Mummy tana kuka, don Abban Abuja ya taho dasu. Ya yi murmushi ya ce, “Zamu je mu lallashi Mummy ta daina kuka”. An ce “mai Da, wawa..... sai Amiru ya karaso a hankali, ya mikawa V.C hannu, suka yi musabaha, aka rasa wanda zai fara janye hannunsa. Dai-dai sanda Baffa ya fito, ya yi musu jagora zuwa falon ganawa da bakinsa. Kallo daya zaka yiwa Alh. Abbas, ka san cewa shima a rikice yake, ya debo gorar ruwa da tambulan cikin firij ya baiwa kowannen su. Aka rasa mai fara sha, aka rasa mai fara magana. Har shi kansa Baffan kuwa, kafin Junaid ya yi gyaran murya cike da tausayin Baban Amir da Habib da ya ke ratsa zuciyarsa. Da ganin wannan ‘giant’ kaga wanda ke fama da dingimemiyar soyayya, wadda ta rasa madafa. Yaran sun baibaye Uncle Junaidu sun kwanta a jikinsa. Ya ce, “Baffa na janye niyyata ta auren Maryama! Na hakura har ga Allah na barwa Baban Amir da Habib, ina bayan Maryama ta koma dakin mijinta uban ‘ya’yanta, don samun kwanciyar hankalin kowannen mu. Ba lallai sai na auri Mairo ba shi ne zan nuna ina kaunar ta, a’a, ni da Mairo mun wuce haka, Yaya ne da kanwarsa, alakarmu hadi ne daga Allah, ba don mu yi aure ba. Ina son ‘yan biyu su tashi gaban uwa da ubansu......kamar yadda Maryama ta tashi gaban Innarta da Babanta, ta san dadin iyaye, tasan amfanin su. Nikuma ina bukatar addu’arku Baffa, da fatan dorewar zumunci na har abada a tsakanin mu”. Baffa ya ce, “Allahu Akbar! Allahu akbar!! Wannan shi ne halin GIRMA, halin ‘yan aljannah!! Da gaske ne kai da Mairo kun fi karfin soyayyah!!! Sai ‘yan uwantaka, mun gode da wannan karamci Junaidu, Allah ya biya maka bukatunka na duniya da lahira, ya kara maka daukaka, ya baka duk abinda kakeso a duniya da lahira......”. Amiru ya cira kai ya tsura ma Junaid ido ya ce, “In aka yi hakan, ni kuma na so kaina.......”. Junaidu ya ce, “Ni kuma ba zan auri Mairo alhalin zuciyarta na ga tsohon mijinta ba”. Amiru yace “nayi rantsuwa da Allah! Mairo tayi maka son da ni bata yimin ba, na aure ta ba da son ranta ba, sai a hankali na koya mata soyayyata. Uncle Junaidu kana da matsayi mai girma a gun Mairo, wanda ni bani da shi.....” Junaid ya rausayar da kai cikin jin wani irin frin ciki a zuciyarsa, koda wannan ya tsira ya tabbata ya isheshi rayuwar duniya, yayi murmushi ya ce, “Kauna ce tsakanina da Mairo Amiru ba soyayyar aure ba tun daga ranar dana fara ganinta, a halin yanzu jin nauyin junanmu ya fi yawa, wanda da kyar za mu iya sakin jiki da juna mu yi rayuwar aure yadda ya kamata. Ka yarda ko kada ka yarda, kai Mairo take yiwa soyayyar aure....!” Amiru ya lumshe ido, ya ce, “Uncle Junaid, bani da bakin da zan gode maka....... bani da abin da zan biyaka wannan alfarmar da ka yi min.....” Uncle ya yi murmushi ya katseshi yace, “Kana dashi Amiru!. Mairo ta sha bani labarin soyayyar da kanwarka Amina take yi mata, wannan wadda suka zo mai kama da kai. Ta shaida min cewa maigidanta ya rasu. Ka bani Amina in aura Amiru, don wanzar da dauwamammen zumunci a tsakanin mu”. Cikin al’ajabi Amiru ya ce, “Amina is special a gare ni ko a cikin kannena goma sha biyu, lallai Amina is among the luckiest.... Na taba gayawa Habibu zan roke ka ka bar mini Mairo, ni kuma in baka kannena hudu ba lefe ba sadaki. Na fada ne kawai a fatar baki, ashe Mala’iku sun amsa. Uncle Allah ya kara GIRMA!”. Suka hade hannunsu suka cure kamar ba za su saki ba cike da wata shahararriyar kauna daga Allah, Baffa ya ja su doguwar addu’a suka shafa. Baffa ya ce, su barshi da Mairo, su ci gaba da shirye-shiryen su, yana so zai yi mata ba-zata ne. Suka yi murmushi. *** Kwana ta yi tana gwada lambar Uncle Junaid ba ta samu ba. Ta shiga damuwa sosai. Tsoron ta kada Allah yasa fushi ya yi saboda ganinta da ya yi tare da tsohon mijinta. Abu kamar wasa Uncle har kwana uku babu wayarshi babu kafarsa cikin gidanta, don haka ta yi tattaki har office amma ba ta same shi ba. Shima Amiru ko sallama bai zo ya yi mata ba, ya kwashe ‘ya’yansa ya tafi Abuja dasu ba ta kara jin duriyarsu ba. Da albishir mai dadi ya tari Alh. Abdurrahaman da Hajiya Aisha, ya kuma gaya musu bukatar V.C na auren Amina. Daddy da Hajiya suka yi ta hamdala tare da kara yawaita sadaka. Ko da Amir ya tuntubi Amina ya yi mamakin amincewar ta nan take. Bai san ita tunda ta dora ido a kan Junaidun ba ta kara gane kanta ba. Ya yiwa gidan Habibu tsinke a daren bakinshi ya kasa rufo, zumudin ya gaza boyuwa. Habibu ya dafa kafadarshi ya ce “Angon Harrit ya aka yi?” Ya harare shi ya ture hannunsa daga kafadunshi, ya ce, “Kai komi mai muhimmanci sai kasa iskanci da shakiyanci a cikinsa, to bani goro in baka albishir”. Ya ce, “To bari ina zuwa”. Ya fito jim kadan bayan shigarsa da kwalin ‘Aspen’ da ‘Lighter’, ya zari daya ya kunna ya manna mishi a baki. Da sauri ya ture ya bige hannunsa, tabar ta fadi, ya bi ya take da takalminsa, cikin takaici ya ce, “Wai don Allah Yaya Habibu, yaushe za ka girma ne?” Ya yi dariya ya ce, “Sai ranar da son Mairo ya daina kai ka hanyar lahira, ya daina kwantar da kai a asibiti, wato ranar da ka zama namijin duniya”. Dina ta yi dariya ta ce, “Rabu da shi Amiru, muna nan muna jiran nashi turn din, idan ya gano wata ‘yar kwailar. Irin su Habib ba ciwo suke a kan soyayya ba, rijiya suke fadawa dungurungum su kashe kansu in sun rasa samun wadda suke so....”. Ya ce, “Amma kin yanke ni ke da sirikinki bashi kuka ci, akwai ranar da zaku biya shi”. Amiru ya ce, “Na ma fasa baka albishir din, tunda da Taba za ka hadani, ka jawo min fushin Mairo, ban ji ba ban gani ba......”. Ya kamo hannunshi ya fizge, yana dariya ya ce, “Haba dear.... tuni na ji albishir din, ai Baffa ya gaya min komi yanzun nan, kun yiwa V.C Junaidu fin karfi kun toshe masa baki da Amina”. Ya yi dariya ya ce, “V.C mutum ne mai saukin kai, yadda na zaceshi ba haka yake ba, ya ji tausayinmu ya tallafi rayuwarmu shima Allah ya tallafesa. Bani da abin da zan biya shi wannan sadaukarwa da ya yi min koda na bashi my favourite sister. Wanda na san zai karba ne ba don so ba, sai don kulluwar zumunci a tsakaninmu”. **** Tana shirin fita office wayar Baffa ta shigo, da hanzari ta amsa cike da girmamawa. Bayan sun gaisa ya ce, “Kina gida ne yanzu?” Ta ce, “A’a, ina shirin fita ne zan ba da lacca 8-10”. Ya ce, “To in kin fito ki zo ina son ganin ki”. Ta ce, “Babu damuwa Baffa sai na iso”. Suka aje wayar a lokaci daya. Karfe goma na safe ta fito daga ‘twin-theater’ cikin rakiyar zugar dalibanta, wadanda suka riko mata jakar hannunta da takardunta har zuwa inda ta adana Terrain din ta, ta karbi kayan hannunsu suka yi sallama suka koma, ita kuma ta zaburo mota sai Yakasai gidan Alh. Abbas. Bayan sun gaisa da Habiba da Hajara da su Rahama, ta samu Baffa a falonsa, ya nuna mata waje ta zauna, ta zamo daga kujera ta dira gwiwoyinta a kasa ta gaida shi. Ya amsa yana duban ta sosai, ganin yadda ta ramar da kanta cikin ‘yan kwanaki kalilan saboda damuwa. Bai nuna mata komi game da zuwan Junaid da Amir ba, tambaya ta farko da ya watso mata ita ce. “Mairo maza biyu za ki aura ne???” Ta cira kai da sauri ta dubi Baffanta, ya girgiza kai ya ce, “Yo maza biyu mana? Kin amshi maganar Junaidu, an gama komi sai shafa fatiha kadai ya rage, sai kuma ki turo min Alh. Abdurrahaman da kansa ya zo bikon ki? Sannan shima Amiru ya zo, dukkanninsu da rokon a maida aure. To dukkansu akwai mutunci da ganin girman juna tsakanina dasu. Don haka bana bayan kowa, zabi yana gare ki, kamar yadda shari’a ta baki dama. Ina so ki gaya min wanda kika fitar ni kuma ranar da na sanya ba zan daga ba zan daura aure”. Kanta a sunkuye ba ta yi magana ba, har sai da Baffa ya gama yana sauraron ta. Ganin ta ki yin magana ya ce, “Kefa nake saurare Mairo”. Daga can kasan makoshinta ta ce, “Baffa ni bani da zabi a cikinsu, kamar yadda ka ce sharia ta bani damar in zaba, ni kuma na baka wannan damar, ka daura da duk wanda ka ga ya dace. Duka ina son su ina kaunar su, don haka ba zan iya zaben daya a cikin su ba”. Baffa ya girgiza kai yana murmushi. Autar Inna Hure, bai san sanda zata daina yarinta ba!. Ya ce, “To shi kenan, tunda haka kika ce, na kuma gode da wannan GIRMA da kika bani, ya nuna min cewa kin amince ba zan yi miki zaben tumun dare ba. Da fatan duk wanda na zaba miki a cikinsu za ki yi min biyayya shima ki yi masa, ba tare da an tsaya yin wasu tone-tone da kwakulo laifin da ya riga ya shige ba, za ki zauna lafiya dashi har karshen rayuwarmu”. Kanta a kasa ta ce, “Na yi wannan alkawarin Baffa”. Ya ce, “To tashi ki koma kan aikin ki, Allah ya yi miki albarka”. Cikin zuciyarta ta ce, “Amin”. Ta taso ta fito kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki. Daga Amiru har Junaid ba ta kara jin duriyar kowa ba. Ta bi shawarar Nabilah, da ta ce dukkansu kar ta neme su ta rabu dasu. Sai ana i gobe daurin auren da ba ta san da wa Baffa zai daura ba a cikinsu. Text din Uncle Junaid ya shigo cikin wayarta da misalin karfe uku na sulusin dare. Ta zaro wayar daga karkashin filonta, hannunta na rawa ta duba, ga abin da ke rubuce. SAKON UNCLE JUNAID GA MAIRO! “Marriage is much more important than mere relationship. It’s the root of all family tree. Any mistake in sowing the seed will be disastrous.... a mature seed has better chances for germinating than an immature one.... A garden close to one’s home has to be watered and tendered than that which is very far away................... -Mai son ki. (wato aure yafi muhimmanci fiye da dangantaka kawai. Domin shine jijiyar bishiyar iyali gaba daya, don haka hadari ne babba asamu kuskure wajen dasa wannan bishiya.... kosashshen iri zai fi saurin yado fiye da talalabuwa.... lambun da yake kusa da gidan ka zaka fi bashi ruwa da kulawa, fiye da wanda yake nesa.............). Ta karanta ya fi cikin carbi, kafin ta fahimci me sakon Uncle yake nufi. Yanzu ne ta fahimci ashe duk sakonnin nan da ake turo mata tana Michigan da ‘logo’ na hular ilmi, ashe Uncle Junaidu ne. Ta kifa kai cikin filon ta, tana kuka mara sauti. Kukan tausayin Uncle Junaidu! A lokacinda ta fahimci Uncle Junaid ya sadaukar da soyayyarshi ga aurenta da ‘ya’yanta..... Ta yadda har ya kira alakarsu da ‘mere relationship’. Ita ma ta yarda ta amince AMIRU SHI NE ZABIN ALLAH, ba zabin zuciyarta ba......!!! [8/20/2019, 06:30] Meema: Daga kowanne bangare ba su samu matsala ba, sun samu kwarin gwiwa daga Baffa, Yaya Habibu da Alh. Abdurrahman Gaya. Wadanda burinsu kenan. Hatta Hanan wadda ke da 'ya'ya biyu a lokacin da mijinta Ramadan ta samu halartar walimar maida auren Dr. Mairo da Amirunta, Amina da Uncle Junaidu, wadda aka gabatar a ranar asabar, juma'a, ashirin ga watan maris, daruruwan jama'a suka shaida daurin auren Mairo da Amiru a karo na biyu, a kofar gidan Alh. Abbas mai goro. Wannan aure ya ga kusoshin ilmi, daga Kano da wajenta, da daukacin jami'o'in Najeriya. Furofesoshi, kwamishinoni da daktocin ilmi, abin ba a cewa komi. Daga Mairo har Ameeru babu mai ra'ayin bidi'o'i, dokance suke da a sake mallaka musu juna. Tsohuwar soyayya ce ke aiki tare da taimakon sabuwar soyayya. Ta dankawa Alh. Abdurrahman da Hajiya Aisha jikokinsu kamar yadda suka nemi alfarmarta, sai fatan Allah Ya ba ta wasu masu albarka. Tana nan zaune a bakin gadonta, tana jiran angon wanda ke can yana ganawa da bakinshi, tare da duba agogon hannunta. Rabin awa kenan da fitar Dina, ta fada bayi ta sake sheko wanka mai suna wanka, tunda kuwa ba ta taba yin irinshi a rayuwarta ba. Ta feshe jikinta da 'fehrenheit' da 'cerruti' dinta kamar yadda ya ke a al'adarta. Tana kokarin sanya kayan barci ya turo kofar ya shigo cikin bulalen 'pyjamas' yana rike da wani dan fulas mai tsananin kyau. Kunya ta kama Mairo, kamar bata taba sanin Amirun nata ba, wanda hakan ya janyo ta sanya rigar a bai-bai. Amir ya yi murmushi, ya rausayar da kai ya iso gare ta, ya ajiye filas din hannunshi a gefe, ya dora kanshi a dogon wuyanta. At last! Sa’ar tashi ce a karo na biyu. Gashi ga Maironsa, bayan gushewar shekaru uku kwarara, cikin duniyar kuntatacciyar soyayya. Shikuwa me zai yiwa Uncle Junaidu, ya biya shi a wannan duniyar? Babu, sai adduar Alheri. Kyawawan fuskokinsu suka zahhara cikin mudubin. Dukkansu suka saki sassanyar ajiyar zuciya mai nauyi. Wadda ke cike da godiya ga Allah! Cancarakas! Ya dagata ita da filas din da ya shigo da shi sai 'bed-room' dinsu. Ya zaunar da ita a bakin gado, ya mika mata filas din, ya ce. "Sako ne daga Nabilah, ta ce hannu-da-hannu na baki. Ya zama shi ne cimarmu a wannan daren, sai dai ban san ko mene ne a ciki ba". Ta soma kicin-kicin bude filas din, da kyar ta samu ta bude. Suka bi cikin filas din da kallo dukkanninsu. “Kwadon Rama” ne wanda ya ji kuli-kuli, tumatur da albasa sai kamshi ya ke. Dariya ta kama Mairo, don ta lura Nabilah dai na son a TUNA BAYA…..... ne. Mairo ta soma cin kwadon ramarta sosai, kunnenta kamar ya tsinke don dadi. Ta kusa cinyewa ya rike fulas din, ya rausayar da ido yana yi mata kallon nan nasa da shanyayyun idanun nan nasa, wanda ya kassara kuzarin jikinta. Ya tada wani tsohon al'amari, wanda ya riga ya shude a tsammaninta. Amir da Mairo, suka ce “Takori kauce a nan, yau bama bukatarki”. *** Washegari Daddy yayi kiransu, ya danka musu ‘passport’ dinsu, mai dauke da visar kasashen duniya guda uku; Athens, Amsterdam da Pretoria. Yace da Amir yayi amfani da hutun sa na karshen shekara suje su huta tsayin watanni uku. Mairo bata tashi dawowa ba, sai da guzurin ciki watanni biyu dan Pretoria. Bayan sun dawo ta nemi chanjin wajen aiki zuwa jami’ar Abuja, ba da son ranta ba, sai don ta samu kasancewa full-time da mijin ta. Abin son ta. Uban ‘ya’yanta kuma abin kaunarta; Dan Abdurrahman Gaya. A shekarar ne kuma akayi bikin kaddamar da Amiru Abdurrahman matsayin gwamnan CBN, bayan gwamna mai ci a lokacin yayi ritaya. Ba don shekarun shi sun kai ba, sai don kwarewa da sanin makamar aiki da dimbin tagomashin cigaba da ya kawowa Central Bank of Nigeria a matsayinsa na tsohon ma’aikacin World Bank. Shima Uncle Junaidu ya samu ‘promotion’ zuwa ‘chancellor’ na jami’ar Bayero bakidaya. Zumunci da aminci bai taba yankewa tsakanin su ba. Shekara na zagayowa Mairo ta direwa Hajiyar Amiru wani saitin 'twins' din data zabi a bawa sunan (Ilham da Sagir) kannen Uncle, don bazata taba mantawa da kaunar da Ilham ta nuna mata ba. Uncle yaji dadi kwarai kuma ya kawo Ilham daga Wales don kawai taga takwararta. Farin cikin Hajiya Aisha abin ba a cewa komai. Dina ma ta sake samun Hurairah (Hure) bayan fidda rai. Amina ta samu Atiku, Ikhlas ma matar Uncle ta sake haihuwa. To haka Nabilah duka hayayyafa suke kamar kaji, sai mu ce Allah Ya raya, kuma Allah Ya kara dankon zumunci. MASHA ALLAHU LA-KUWWATA ILLA BILLAH... Maman Safah da Marwah ce....ke cewa. Sai mun hadu a sabon littafin YAKANAH cikin yardar Maiduka. Dandano Daga Yakanah Karfe goma sha dayan dare garin kano yayi tsit, sai iskar hunturu dake kadawa. Malam Ja’afar ya dauko tabarmar sa ya shigo cikin gida daga soron kofar gida. Zai gitta ta dakin Fati ya jiyo sheshshekar kukanta. Ya dakata, ya dago labulen yana kallonta. Tana zaune akan darduma ta kunshe fuskarta cikin hijabi sai kuka take. ya karashe shigowa cikin dakin yace “Fadimatu kukan me kike yi? A razane ta cira kai ta dube shi idanunta jawur sun yi luhu-luhu alamar tayi kuka har ta gode Allah. Malam Ja’afar ya zauna a wata ‘yar kujera dake dakin yana fuskantar diyarsa. Ta share idonta da hankici, ta ja shashsheka kafin tace “Baba babu komai” ya jima yana kallonta sannan yayi murmushi yace “kina tuhumar mu dayi miki auren da baki so, auren mijin ‘yar uwar ki. Ki yi hakuri, alheri muke nufin ku da shi, ba zaki gane ba sai nan gaba. Idan kun gano gatan da muka yiwa rayuwarku” Fati tayi shiru tana sauraron babansu. Taga wannan itace damarta ta karshe. Daga gobe za’a zarga mata igiyoyin wanda baya sonta. Ta kai kanta kasa tana kuka sosai tace “ku yi min alfarma Baba. Baba baka taba sa ni in yi wani abu na shallake maganarka ba. Amma a wannan karon ina so ka dubi hujjoji na. Baba. Dr Sulaiman baya so na, baba Dr. Sulaiman yafi karfi na. bani da ilimin da zan jera da shi a matsayin matarsa. Baba sulaiman bazai taba son wata ba bayan son da yake yiwa yaya Hadiza. Baba kune baku sani ba, amma Dr. sulaiman ya tsaneni ban san laifin da nayi masa ba. Ban taba gaishe shi ya amsa ba, haka bai taba kallona a matsayini jinin Hadiza ba balle yayi la’akari da wannan ya kaunace ni. In dai don ‘ya’yanshi ne, ai nima ‘ya’yana ne…zan cigaba da rike su ba sai na zama matarsa ba……” Ya ce “Amma zaki zama matar wani ko? Kuma babu wanda zai aureki da zugar ‘ya’yan yayar ki. naji hujjojin ki Fati, amma nima ina so in tambayeki “wane abu ne Hadiza take da shi wanda ya kaita ga matakin zama matar Babban likita irin Sulaiman???? Tana ‘yar talakawa kamar ki??? Mu biyo Fati da Babanta a littafin YAKANAH yana zuwa bada jimawa ba!!!! __________-_TAKORI