*_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑃𝑎𝑔𝑒 𝑜𝑛𝑒_ _Free page_ *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan ALLAH, Mai rahama, Mai jin ƙai._ .........Humm wato Bilyn Abdull atawa fahimtar da abinda shekaran jiyata da jiyata har zuwa yau ɗina tazo min dashi zan iya cewa JARUMTA itace asalin RAYUWA. HAƘURI shike jagorantar numfashi da samun tsahon rai ga kowanne halitta a cikin salama. A duk sanda wasunmu suka tambayemu minene adonmu? Amsa ɗaya muke fara kallo a zukatanmu da furuci (TARBIYYA). Sai dai a gareni ni nace sam ba haka bane. Zan kuma iya faɗa a hankali ko da amsa kuwwa harma da shelantawa. Kada kai mamaki ko fahimtata a bisa tsatstsauran ra'ayina ko zama mai bahagon hasashe. Bance tarbiyya bazata amsa suna ADO ba, sai dai magana ta gaskiya ADDINI shine mafi girman zama ƙololuwar ADO a waje na. Sannan akai kanka da ku kanku duk shine. Ina tsaye bisa wannan ra'ayine saboda ina girmama ADDINI NA bisa koman dake amsa komai na a rayuwa. DUNIYA itace MAKARANTAR farko ga kowanne ma'abocin numfashi, domin a cikinta ake fafutuka da hanƙoron neman SAKAMAKON zuwa MATABBATA. Sobada a yanda ka tafi da ita a haka take baka daraja da kima a wajen komai da kowanka. Kowanne mai numfashi yana tsoron MUTUWA, amma hakan baya hanamu buƙatar RAYUWA da fatan shiga ALJANNA, saboda a canne ake iya samun komai da komai da zukata basa iya hasasowa koda da tsayin motocin hange. Haka zalika ƙarewar kwanakin numfashinmu a kowanne wayewar gari baya hanamu sake tanadin BURIKANMU koda kuwa yaƙininmu na nufin baza muga GOBENMU BA. Duk wani ɗan adam zakiga RAYUWA na taka masa iya rawar abinda littafin ƙaddararsa tazo da shi ne kawai, duk kuma iya hanƙoronka da faɗi tashi akan neman DUNIYA ko guje mata baka isa zartama wannan ƙaddarar taka ba.        Kar na kaiku da nisa bara na baku komai a buɗe a yanda zaku fi fahimtar abinda nake son faɗa ga Bilyn Abdull da ku baki ɗaya. Sunana shine *_SAMRAAH ABDUL-WAHAB GWARZO_*. A zahirin rayuwa ni ɗin ba kowa bace face ɗiyar Malam Abdul-wahab Gwarzo. Domin kuwa mahaifina bai kasance mutum mai mulki ba, haka ba attajiri bane, ba kuma babban malami ba. Shi ɗin driver ne dake aikin tuƙi a wani gidan attajirai. Sai dai ALLAH yay masa rasuwa sakamakon haɗarin mota tun inada shekara bakwai a duniya. Mu uku kacal ya haifa shi da mahaifiyarmu da itama dai ALLAH yay mata rasuwa bayan haihuwar ƙanina tun bamma cika shekara uku a duniya ba. Yaya Musaddiq shine babban yayanmu, sai ni Samraah da autanmu Hafizzullah. Tun bayan rasuwar mahaifiyarmu riƙona ni da Hafizzullah ya koma hannun ƙanen mahaifiyarmu Uncle Imam. Matarsa ita ta ƙarasa shayar da Hafizzullah tare da yaronsu data haifa itama kusan lokaci ɗaya da mamanmu, sai dai bamu da tabbacin ma kota shayar da shi ɗin ko batayi ba. Dan haka suka tashi tamkar tagwaye. Bayan rasuwar mahaifinmu riƙon Yaya Musaddiq ma ya dawo hannun Uncle Imam. Duk da mahaifinmu bamai arziki ko mai mulki bane ya tafi ya barmu da gonakin gado harma da gidan zama. Sai wasu ƴan kuɗaɗe a account. Itama mahaifiyarmu tabar mana gonaki data gada a wajen nata iyayen tare da Uncle Imam dan su biyu kacal iyayensu suka haifa suma. Kasancewar duka iyayenmu a cikin garin Gwarzo suke waɗan nan dukiya tamu duk tana acan ne. Sai gida da muka rayu kawai anan cikin birnin Kano. Karancin shekarunmu yasa duka abinda iyayenmu suka bar mana bayan an raba mana shi ba'a bamu ba, acewar Uncle Imam sai mun girma dan duk shi ya ɗauki komai ya ajiye, gonaki ya cigaba da nomasu, gida ya saka ƴan haya. Uncle Imam shine ya cigaba da ɗaukar nauyin karatunmu dama dukkan al'amura na rayuwarmu har sanda muka kawo girma. Duk da dai rayuwa a gidan Uncle Imam bata taɓa kasancewa mai sauƙi a garemu ba saboda mugun halin matarsa duk mun shanye wannan a ranmu. Amma tabbas mun ɗanɗana kuɗarmu a hannunta akan abubuwa daban-daban. Mun fuskanci ƙalubalen maraici kala daban-daban. Dan komai da zasuyi ma ƴaƴansu yanada bambanci da wanda mu za'a mana. Hatta da abinci takan fifita ƴaƴanta akan mu. Hakama a makaranta suna private school muna government school. Sutura akoda yaushe tasu nada banbanci da namu. Hatta da ɗakin kwana na yaransu nada banbanci da namu. Abin zai baka mamaki idan nace duk wannan wariyar launin fatar muna ganine har daga Uncle Imam bawai ita kawai ba. Kafin mu san kammu mukanyi kuka mu share hawayenmu, bayan mun mallaki hankalinmu musamman ma ni sai na fara maida murtani. Nakan shanye daga ƙyara da hantarar Mom da Abba. Amma bana iya kauda kai daga al'amuran ƴaƴansu. Dan hatta waɗanda suka girmeni idan suka nuna min yatsa saina karya shi nake samun nutsuwa koda za'a rama musu ne. Amma ga Yaya Musaddiq ba haka bane ba, dan shi mutum ne mai shiru-shiru, hakama Hafizzullah baida yawan hayaniya. To nima ɗin dai a zahirance bazakace ina magana ba, dan banda yawan surutu, sannan inada yanayin fuskar salihan mutane. Shiyyasa sometimes nakan aikata abu Mom ta faɗa ace ba'a yarda ba, ni ɗin nan dako yatsa aka saka min a baki bana ciza ba. Wannan halayya tawa na ƙona mata zuciya da ruhi, dan haka nafi sauran ƴan uwana cin wahala da azaba a hannunta harma da hannun Abba ɗin. A haka dai muka rayu cikin haƙuri da juriyar rayuwa har ALLAH yasa muka kammala secondary. Daga nan Abba yace baida kuɗin biya mana mu cigaba da karatun jami'a. Raina ya ɓaci matuƙa domin ganin yanata cuku-cukun biyama Abbas ɗansa dake sa'a da Yaya Musaddiq, da Baby mai sa'a dani. Dan haka na sameshi da batun tunda hakane ya biya mana da gadonmu. A saida gona guda a biya mana. Maruka nasha lafiyayyu masu gigitarwa a wajensa, daga ƙarshe ya koroni da zagi daga falonsa. Duk da ran Yaya Musaddiq ya ɓaci shima baice komai ba, saima faɗa daya shiga min akan abinda nayi. Acewarsa baikamata nayi magana ba, dan koba komai Abba ƙanin mahaifiyarmu ne, ya kumayi wahalar riƙemu kafin yau. Komai bance masa ba, face hawaye kawai da nake zirararwa. Shima bai sake cewa dani komai ba ya fice a gidan.       Kwanaki biyu da faruwar hakan Yaya Musaddiq yazo min da labarin ya samu wajen aikin koyon kanikancin motoci. Duk da ni ba haka nake buƙata ba karatu nake son muyi sai na tayashi murna kawai da fatan alkairi. Daga lokacin Yaya Musaddiq ya fara zuwa gareji, dan koda ya faɗama Abba sai bai wani maida hankali ba face cemasa ALLAH ya bada sa'a a daƙile. Su Baby sun fara zuwa makaranta, yayinda ni kuma na koma mai aikin gidan. Dan dukkan wani aiki na cikin gidan a yanzu ya koma kaina ne gaba ɗaya har wanda banayi a da. Sai idan Hafizzullah ya dawo yake kama min da wasu ayyuka. Ina matuƙar jigatuwa, amma hakan bai hanani shiryawa na tafi islamiyya duk rintsi kuma koda za'a dakeni ne. Tun ma idan na sulale naje na dawo Mom kan dake ni har ta haƙura ta tattarani ta watsar, sai dai dolene bazan fita ba sai na kammala duka aikin data bani, samun wannan damar ya sakani jajircewa na gama komai akan lokaci dan na wuce. A wannan yanayin shekara ɗaya ta shuɗe da kammala sakandare ɗinmu, na samu nasarar yin saukar Alkur'ani, sai dai babu abinda akaimin na walima sai wanda Yaya ya ɗan mun, ban kuma damu ba. Yayinda su Baby keta zuwa makaranta, Yaya Musaddiq na jelen zuwa gareji. Dan in ya fita tun safe sai yamma yake dawowa. Da farko Abba bai damu da aikin Yaya Musaddiq ba balle abinda yake samu, sai daga baya da Mom ta zugashi wai yana samun kuɗi tunda yamun ɗinkin walima sai ya sharɗanta masa yo cefane kullum a gidan. Duk da hakan ya zafi Yaya Musaddiq saboda shi yanada burinsa akan shiga aikin bai nuna ba ko'a fuska, sai ya koma raba kuɗin da yake samu biyu yana ajiye rabi kamar yanda ya saba rabin yana cefanen. A wata ranar da tai dai-dai da cikar shekarar mu ɗaya da watanni biyar da gama sakandire sai ga wani malamin mu yazo neman Abba. Bayan sun ɗan gana na wasu mintuna akai kirana. Ranar da bazan taɓa mantawaba kenan a rayuwata, ranar data zama komai daga cikin TSIRON da yazama shine TUSHEN LABARINA. Ranar da ta zama MAFARIN da har yau ba'a kai ga zuwa ƘARSHE ba tunda numfashi bai rabu da gangar jiki ba.......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒐_ .......Mal Saminu yazo da daddaɗan labari garemu cewar na samu scholarship na cigaba da karatuna. Misalta muku yanda na shiga ɗunbin farin ciki a wannan ranar ni da ƴan uwana guda biyu ɓata lokaci ne. Yayinda Abba da Mom da su Baby suka nuna baƙin ciki da hassadarsu a fili akan hakan. Dan da farko ma Mom catai ƙarya ne babu inda zanje, Abba kuma ya goya mata baya, sai da Malam Saminu ya tabbatar musu da in har aka hanani akwai matsala. Dan kuwa gwamnati zata iya bibiyar al'amarin ta kuma hukunta duk wanda yay uwa yay maɗaukiya akan hakan. Jin wannan bayani ya sakasu barina dole nima a wannan shekarar aka shiga damawa dani a harkar karatu a B.U.K. inda Baby da yayanta Abbas suke nasu karatun suma.                 *_MATAKON FARKO_*    Uhm dole a kira wannan ajin da matakin farko. Domin kuwa akansa ne komai ya fara, farawar da kamar itace farkon buɗe shafin rayuwata ta hankali, domin kuwa ko babu komai shekarata goma sha bakwai a yanzu. Zan iya cewa na shiga jami'a a sa'a. Domin kuwa course ɗin da nafi so da buri shina samu. A shekarar farko dana fara karatuna na fahimci halin da Baby ke ciki a school ɗin. Dan kuwa tuni ta ajiye karatu gefe sune shegun makaranta. Iyaka su shiga ofisoshin malamai su ɓata lokaci wani lokacin ma harda gidajensu ko a ɗaukesu a mota a fita da su, batun karatu kuwa sam babu shi tare da su, sunada group kuma. Amma abin mamaki sunansu na gaba-gaba a allon kafe jarabawa matsayin wanda suka cinye komai sai ɗan abinda ba'a rasa ba. Ga Yaya Abbas ɗin ma bata sauya zani ba. Dan shima ɗin dai yafi maida hankali ga siyasar makaranta da bin abokai masu motoci fiye da karatun. Bayan Yaya Musaddiq ban taɓa sanarma kowa a gidanmu ba, shima kuma tunda ya kwaɓeni akan hakan ban sake kawo masa zancen ba na maida hankali ga karatu na. Ina a wata na biyar da zuwa mukai karan batta da Mansoor. Mansoor Khalil Musa matashin yaro ɗan ƙwalisa. Ƙyaƙyƙyawan gaske mai tarin ilimi. Yana shekararsa ta uku a cikin b.u.k. A yanda Mansoor ke shigar suturu na alfarma da mota zai tabbatar maka da shi ɗin ɗan masu hannu da shuni ne. Sai kuma ƙwazonsa da ƙyawunsa ya sake jan hankalin ƴammata na cikin makarantar da yawa a kansa. Sai dai sam bai ɗaga ido ya kalli kowaccensu balle ya yarda magana ta haɗasu. Hakan yasa ake masa laƙabi da mutum mai girman kai. Domin kuwa bayan abokansa biyu babu wanda yake kallo da gashin arziƙi a ɗaliban dake ƙasa da shi harma wanda ke sama da shi. Amma sai me rana ɗaya ALLAH ya haɗamu a cafeteria. Muna tsaka da cin abinci ni da ƙawata ɗaya tilo Joy muna hirarmu cikin nishaɗi ya shigo tare da abokansa. Duk da yanda naji cafeteria ɗin ta ɗauki gunaguni a kansa banko kalla sashin da suke ba. Sai kawai jin abokinsa mukai kammu cikin gadara yace wai mu tashi zasu zauna. Cikin tsoro Joy tai niyyar miƙewa, amma sai na balla mata harara batare da nace komai ba. Zungurina tayi cikin roƙo da magana ƙasa-ƙasa ta ce, “Please Sam Gee mu tashi, ni sam bana son fitina. Kin san kuma halin guys ɗin nan ba mutunci ne da su ba”.        Kai tsaye na buge hannunta a fusace da faɗin, “Idan kinga na tashi a wajen nan na gama abinda nake yi ne Joy”. Daga haka na cigaba da cin abinci na. Zaram Joy ta miƙe, amma a mamakinmu dama duk mutanen dake wajen sai muka tsinkayi Mansoor na faɗin ta zauna abinta, cikin rashin damuwa yaja kujerar kusa dani ya zauna shima. Hakan da yay ya bama kowa mamaki, duk da dama bawai an taɓa ganinsa yana faɗa da wani bane ba, kawai dai an sanshi shi mutum ne mai girman kai da rashin shiga shirgin kowa, abokansa ne masu zuba rashin mutuncin ga kowa. Dan ko magana ma sai yaso yayita da mutum. Suma abokan nasa zama sukayi bayan sun musu order ɗin abinda zasu ci, ko gezau banji ba, ban kuma kalli kowannensu ba harna kammala cin abincina na miƙe bayan na saki niƙab ɗin fuskata. Dan kullum nakan shigo makarantar ne cikin hijjabi har ƙasa da niƙab, ko kuma nurse mask da eyeglasses, dan haka ba kowa ne zai iya shaida maka fuskata ba hatta ƴan department ɗinmu ma. Hasalima sunan Hijjab girl na neman bina, dan kowa idan zai kwatance da sunana yakan kwatantani da hakan ne. Idan ka cire Joy da ke kirana da *_Sam Gee_*. Mun bar wajen yayinda mutane keta ɗan ƙusƙus ɗin magana, kun san dai ɗalibai da rashin raina abin kace nace, yayinda Mansoor ya bini da kallo tamkar ya samu television. Tun daga wannan ranar al'amarin kamar wasa, sai ya zam a duk sanda mukaje cafeteria cin abinci Mansoor da abokansa zasu zo. Kuma koda tare muke da wasu a tebiri sai sun tashesu sun zauna. Ban taɓa tanka musu ba balle nuna nasan sunayi har muka shafe kusan sati biyu a haka, kafin shi Mansoor ɗin da kansa ya fara biyan kuɗin abincin da duk muka amsa a kullum. Anyi na farko anyi na biyu a ran ta uku na taka masa birki dayin hakan cikin masifa da kowa bai san na iya ba, amma maimakon yaji haushi sai yay murmushi kawai ya tashi ma ya bar cafeteria ɗin abinsa. Naji haushi amma sai na dake, na kumayi alƙawarin saboda shi bazan fasa zuwa cafeteria ɗin cin abinci ba, yayinda shi kuma bai fasa biya mana ba, kuma koda mun biya ba'a amsar kuɗinmu sai ace ai anbiya mana. Abin na ƙona min rai, na kuma rasa yanda zanyi, ina kuma akan bakana na bazan daina zuwa cafeteria ba. Tun ina jin zan sharesa har na fara magana, nan ma a banza, sai kawai na daina dan na fahimci maganar tawa ke tunzurashi kamar. A haka muka cinye wata guda. Abu dai kamar wasa sai ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai shaƙuwa ta fara shiga tsakaninmu da Mansoor da abokansa. Takai idan ma basu zo cafeteria ɗin ba nakanji babu daɗi, kamar yanda shima yakanji idan bai ganni ba. Abinda zai baki mamaki kuma har lokacin ba wata doguwar magana ke shiga tsakaninmu ba, gaisuwa ce kawai sai zaman cin abinci.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_ ......Tun dai muna shashshare juna har abinda ke cikin zuciya ya bayyana, domin kuwa Mansoor ya fito fili ya nuna min shifa sona yake. Tom kun san dai halin mutuniyar taku, ban gusa ba na balbalesa da masifar da zuwa yanzu wasu sun fara kallona da sumumu kasau macijin sari ka noƙe. Maimakon yaji haushi sai ya dinga sakar min murmushi, wannan shine karo na farko da nabar zuwa cafeteria da tunanin ai Mansoor zai ƙyaleni na huta, dan ni kam burina karatu ba soyayya ba. Sai dai kuma ba hakan bane ba, dan kuwa dai shima salo ya canja ta hanyar nuna ba soyayyar za'aiba yanzu karatu ne gaba, idan komai ya daidaita nan gaba sai soyayyar ta koma gaba. Tun ina shashsha masa ƙamshi harna miƙa wuya. Kafin wani dogon lokaci kowa yasan soyayyar mu da Mansoor kasancewar sa mutum popular a cikin makarantar, duk da dai kamar yanda ta faɗa karatune gaba ba soyayya muke ba, dan da wahala ma kaji ya saka min batun soyayya, sai yayta amfani da hakan shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tdakaninmu. Komai ya cigaba da tafiya yanda ya kamata, Mansoor na taimaka min matuƙa a ɓangaren karatu ni da ƙawata Joy. Hakan kuma ya sake fiddo ƙwazona. Sannan soyayyarsa na bani kariya sosai daga tsagerun ɗalibai harma da malamai ƴan bani gishiri na baka manda. Tun sauran ɗalibai na ɗaukar soyayyar yaudara ko wata manufa har suka yarda ɗari bisa ɗari da gaske muke, saboda komai muna gudanar da shi a tsaftace.        Tafiya tai tafiya, shekaru sunja abubuwa sun canja. Su Mansoor sun kammala karatunsu, sai dai kuma muna nane da juna ta waya. Yana kuma zuwa gida duk da ban taɓa yarda kowa yasan da batunsa ba bayan Yaya Musaddiq. Koda yake su Baby sun sani, dan nasha jin ma wai ai Baby ta jima tana son shi, sai dai bansan minene ya faru koya katangeta da sanarwa a gida ina soyayya da wani ba, sannan ita bata taɓa tarata da batun Mansoor ba kai tsaye, sai dai tai habaici a wasu lokutan ko shaguɓe, ni kuma sai ban taɓa kulata ba ko nuna na fahimta. Ina zangon ƙarshe na kammala karatuna na fahimci ashe Yaya Musaddiq shike biyamin kuɗin makaranta babu wani scholarship dama. Ya haɗa baki da malamin namune kawai, dan a yanzu haka shima Hafizzullah yana a level 100 a jami'ar Umaru Musa ƴar-aduwa dake Katsina. Shima kuma dai da batun scholarship ɗin nan aka rufe bakunan su Uncle Imam duk da an kwashi tashin hankali sosai fiye da nawa lokacin kasancewar shi Nabil bai samu ya tafi ba har yanzu. Ranar da nasan wannan sirrin nasha kuka a gaban Yaya Musaddiq. Shiko ya dinga lallashina yana murmushi, a ranar ya sanar min da komai bai ɓoye min ba. Dan yace bazai taɓa iya zama bamuyi karatu ba, dan haka ya zaɓi bi ta wannan hanyar domin gina gobenmu. Shiko aikin kanikancinsa ya ishesa in sha ALLAHU. Na nuna masa ban yarda ba, shima dole ne musam yanda zamuyi ya koma karatu, dan kuwa zuwa yanzu yana samun kuɗi sosai, sai dai duk a hidimar gidanmu da karatunmu suke tafiya, dan har yanzu bai tsinanama kansa komai na rayuwa ba irin burin matasa na son gina gida da sauransu, hatta budurwa ma baida ita shi sam. Ya min alƙawarin idan lokacin komawar yayi zai koma in sha ALLAHU.       Alhmdllh na kammala karatu cikin nasara, yayinda na riga Abbas da Baby da suka rigani farawa kammalawa saboda su sun saka wasa a karatun nasu. Bakuma su da niyyar gama school ɗin da alama, maybe sai an korosu su shiga hankalinsu oho, dan gasu nan koda yaushe cikin maimaita shekara suke. Bayan kammala karatuna da wasu watanni Mansoor yay uwa yay maɗaukiya ya sama min aiki a wani gidan tv da rediyo dake tashe a wannan lokacin. Hakan ya saka Yaya Musaddiq farin ciki, yayinda ran su Abba yay baƙi har suka kasa ɓoye hassadarsu a fili musamman ma Mom, dan da farko ma tuburewa tai akan tunda na gama karatu aure kawai ya kamata Abba yay min, wai akwai wani ɗan yayarta ya jima da cewa yana so na. Abba har ya ɗauki zancenta da muhimmanci niko na tibire nace wlhy idan aka aura min shi kashesa zanyi, dan ni ban shirya aure ba sai na fara aiki na. Ganin fa da gaske nake kuma sun san tsurin idona dan randa yaron yazo hira wajena zagin ƙare dangi na masa, hakan yasa Abba ya kashe maganar, sai dai ban san yaya sukai da matar tashi ba a ɓoye, a zahiri dai yace ya kashe wannan batu naje nai aiki na. Amma ya bani nan da ƙarshen shekarar nan na kawo miji. Oho ban wani damu dasu ba na fara aiki na, dan nasan dai inada Mansoor ɗina a hannu. Cikin nasara kafin kace mi na samu karɓuwa, albashina na farko dana biyu dana uku na haɗa da shi na sayama Yaya Musaddiq fili da taimakon Mansoor. Lokacin dana damƙa masa takardun sai kawai ya fashe da kuka. Nima kukan na fashe da shi tare riƙe hannunsa ina roƙonsa dan ALLAH ya daina, shifa uba ne a garemu yanzu, idan bamu masa hidima da abinda ALLAH ya azurtamu da shi ba wa zamuyimawa. Da ƙyar dai mukai shiru dan dama a wajen aikinsa na samesa, gudun kada na bashi a gida wani yaji a ƙwace. Tom Alhmdllh, yanzu dai a taƙaice watanni na shida kenan da fara aiki na, ina kuma matuƙar jin daɗin da nuna kwazo matuƙa. Dan bada ƙwaƙwalwa kawai nake aikin nan ba, harda zuciyata da ƙwanjina gaba ɗaya. Gashi ALLAH ya bani farin jinin mutane, dan tunda na fara gabatar da wani shiri akan matasa shikenan kamar nayi kiranyen masoya, dan da a iya rediyo ne kawai, amma wata guda kenan da fara gabatar da shi a television saboda yanda oganmu yaga shirin ya amsu yana sake jawo hankalin mutane ga channel ɗin tamu sai abin yay matuƙar birgesa. Dan haka aka sake ƙarfafa shirin ta hanyar fiddoshi a fanninmu na television ma, Alhmdllh kuma komai na tafiya fiye ma da yanda akai zato da tsammaninsa.......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑭𝒐𝒖𝒓_ ......A gurguje nake faman shiryawa saboda makarar da naso nayi. Ba kuma komai ya jawo min hakan ba sai sharaɗin girka breakfast ga masu gidan a kullum kafin na fita bisa umarnin Mom bayan gyara ko ina. Ban isa nace bazanyi ba, dan na fahimci hanyar da zata tuzguɗe ɗan aikin nawa take nema. Dan haka na tsarama kaina time table ta yanda bazan cutu ba. Kullum ƙarfe huɗu na asuba na tashi, zan shiga kitchen na ɗaura breakfast. Inayi ina ɗan wasu aikin gyara gidan har na kammala, dana gama na maida hankali ga sauran ayyukan, ALLAH na taimakona kafin ai kiran sallar farko zaka samu na kammala komai, da Yaya Musaddiq ya fahimta ma sai ya zam shima yana tasowa muyi tare dandanan saina kammala nai shiri. To yau an samu akasi ne da alama Yaya ya makara, dan har na kammala bai shigoba, gashi ma har na gama shirina. Nayi ƙyau sosai cikin baƙar abayar dana saka, nai rolling veil ɗin ta da ya sake fiddoni tsamm kamar wata ɗiyar larabawa. A ɓangaren ƙyawun fuska dana jiki babu abinda zance sai Alhmdllh, sai dai ban taɓa jin alfahari ko son yin ɗagawa da wannan baiwar da ALLAH yay min ba. Nakan gode masa ta hanyar suturta kaina da ƙyaƙyƙyawar shiga, dan kullum cikin dogon hijjabi nake da nose mask. Dan ƙaryane kace ka ganni babu nose mask a fuska. A lokacin dazan fara gabatar da shirin nan a sashen tv ansha gumurzu dani a ranar farko dan har hawaye saida nayi saboda ciresa, dole dai na haƙura daga ƙarshe ma toshe idona da eyeglasses sannan na iya gabatar da shirin, a hakanma ina jin kaina kamar ba daidai ba.     Kamar kullum mask ɗina na saka, sai dai yau baƙi ne, yay min ƙyau sosai dan ƙyawawan fararen idanuna masu girma da cikar gashi kawai ake iya gani. Cikin takun nutsuwata na fito, ga wani ƙamshi mai sanyi yana tashi a jikina, sai dai bamai ƙarfi bane, dan sai ka kasance a kusa dani sosai zaka iya jinsa yanda ya kamata. Sauri nake, dan haka bana fatan haɗuwa da kowa na gidan. Sai da na leƙo na tabbatar babu kowa a falon sannan na ƙarasa fitowa. Nan ma da sanɗa na fita, inayi ina waigen bayana. Ban sami nutsuwa ba saida na ganni a waje, na sauke nannauyar ajiyar zuciya ina sakin murmushi, bag ɗita mai zubin school bag na rataya hannunta guda a bayana, ɗakin yaya na fara leƙawa, sai muka kusa cin karo dan shima yana niyyar fitowa ne.        “Kandala ƴar jaridan Yayanta”.    Ya faɗa cikin tsokana yana mun murmushi. Murmushin nima na mayar masa ina ɗan rufe fuskata da tafin hannuna. Sai kuma na janye ina ɗan ɓata fuska da faɗin, “Ai ni fushi ma nake da kai yaya. Na manta nai maka murmushi ma.”      Cikin dariya ya ce, “Oh oh Tom ayi haƙuri Ƴar ficika, nasan laifin Yaya dai rashin shigowa taya aiki, wlhy jiya na matuƙar gajiya ne a gareji, shiyyasa tunda na samu na kwanta ko juyi banyi ba sai kawai naji ana sallame salla. Dan yau ma sai a ɗaki nayi tawa dan abin kunya”.      Dariya na ƙyalƙyale da ita sosai saboda yanda yay da fuska kamar wani ɗan yaro. Sai kuma na kalla agogo da sake kallonsa. A zabure na ce, “Uhm Yaya zan makara. Ni dai taho muje ka saukeni, dan yau a mashin ɗinka zanje office, ina son na baka wani labari a hanya”.          Babu musu yace min muje, saboda karna makara bai shiga gidan ya gaidasu kamar yanda ya saba ba. Ya kuma san sai yasha masifa akan haka ɗin, amma yafi buƙatar farin cikina. Cike da farin ciki muka bar ƙofar gidan tamkar bamu da wata damuwar rayuwa. Maganar da nace masa zamuyi na fara masa. Ba komai bane face batun fara gininsa, dan ina son a fara ya samu yay aure. Bai dai ce dani komai ba face murmushi kawai har muka isa, a ƙofar gate ya ajiyeni. Har lokacin fuskarsa da murmushi ya kalleni. Sai kuma ya ɗan ja fasali da harɗe hannayensa a ƙirjinsa yana kallona.       “Samraah!”.    Ya kirayi sunana da tsantsar kulawa. Amsa masa nai nima da girmamawa. Numfashi ya sake furzarwa da ɗan duƙar da kansa ƙasa kamar mai nazari, sai kuma ya ɗago yana sake kallona. “Samraah inaga ba batun gini ya kamata muyi ba yanzu. Kamata yay ace mu tattali abinda muke samu domin kayan aurenki. Kin girma Samraah, kin kammala karatunki cikin aminci, ga aiki kin samu cikin sauƙi, kina da Mansoor a hannu, a ganina batun aure ya kamata ace kunyi da shi yanzu kafin ma lokacin da Abba ya baki ya cika. Kin san dai halin Mom basai na faɗa miki ba, wannan shirun da kikaga tayi wlhy bazai zama na alkairi ba. Gara mu fiskanci zahiri. Wannan ƙaramin jikin naki yabar kwasarki ba baya kike komawa ba shekaru ne ke ƙaruwa. mutanen wajene kawai suke miki kallon ƴar ƙarama ganinki ƴar ficit. Ni nawa batun mai sauƙi ne, namiji ne ni, konan da shakara goma bazan tsufa da aure ba ai. Ga Hafizzullah yanzu ya fara karatunsa, kamata yay har sai shima ya kammala koda zan yi batun wani aure, sai nake ganin kamar hakan zai fi, ni dama ba wata budurwa ba a ƙasa”. Ya ƙare maganar da zolaya.      Baki na kumbura cikin ƴar shagwaɓa nace, “Yaya ni duk ban amshi wannan ƙorafin naka ba sam. Kadai bari mu samu lokaci mu zauna mu tattauna. Amma batun bazakai aure ba sai nayi ko Hafiz ya kammala makaranta duk baima taso ba. In dai Dan budurwar ce zan maka, amma bazan bari ka cigaba dama waɗan can mutanen bauta ba. Kura da shan bugu gardi da ƙwace kuɗi. Wannan lokacin ya wuce muma yanzu munsan kammu”.       Kansa kawai ya girgiza, nasan kuma ba komai ya sakashi yin hakan ba sai ganin yanda na ƙarasa maganar a hasale. A bayyane fushina da zafin mariƙanmu ya gama bayyana. Maimakon yace wani wani sai kawai yaymin nuni da gate alamar naje ciki. Banyi musu ba nai masa sallama na nufi shiga ciki ina kumbura baki da fiki-fiki da idanu najin haushi........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑭𝒊𝒗𝒆_ ........Ina zama office ɗinmu daya kasance mu biyar ne a ciki Asiya data kasance duk tare muke anan ta shigo da sallama. Ganin takardu a hannunta ya tabbatar min da ba yanzu ne ta shigo ba. Gaisawa mukai farko, kafin ta ɗora da faɗin, “Samraah MD na kiranki kuwa. Ya ce ki maza kuma dan zaiyi baƙi”.        Kaina na jinjina mata batare da nayi magana ba na miƙe ina sake gyara zaman facemask ɗina daya ɗan zamo ta saman hanci. A cikin takuna na nutsuwa da yanga da mutane da yawa ke fassarawa na fito. Duk wanda na gamu da shi nakan ɗaga masa hannu da cewa good morning, wasu sukan ɗan tsokaneni. Sai dai iyakata murmushi kawai dan nifa idan ba kayi dogon zama dani ba bazaka taɓa tunanin inada surutu ba sam. Ban cika yawan magana a ko ina ba sai in nice naga damar hakan. Shiyyasa da yawan mutane ke ɗaukata mai shiru-shiru. Har wasu kan dangantani da hakan da iya yardarsu. Basu sani ba idan aka taɓoni banda ragi banda ragowa sam. Na isa office ɗin MD, bayan nayi knocking sai da nai tsaiwar kusan minti ɗaya kafin ya bani izinin shiga ciki. Kallo ɗaya na masa na ɗauke kaina, dan mutum ne shi mai shegen son kallon mutane kamar zai cinyesu. Cikin son kawar da idanunsa dake yawo a kaina ya ce, “Zauna”.       Zaman nayi a ɗarare nace da shi, “Good morning sir”.        A taƙaice ya amsani da, “How are you?”. Batare da ya jira amsawata ba ya cigaba da maganarsa yana turomin wata ƙyaƙyƙyawar mujalla da wani envelope mai kama da invetion card. Bana ganin fuskar mutumin daya mamaye bangon farko na mujallar gaba ɗaya. Sai jikinsa dake sanye cikin wasu shegun suit sky blue zuwa ƙafarsa dake cikin cover shoes dake wani shining duk da kuwa a hoto ne. Zaune yake a kujera ƙafa ɗaya kan ɗaya, hakan ya bani ɗan damar ganin hannunsa mai ɗauke da dogayen fararen farata dake riƙe da glass cup da guntun drink ke ciki. Sai zobe guda ɗaya mai ƙyau sosai a yatsarsa...          Duk da baifi a sakanni goma na ƙarema hoton irin wannan kallon ba a ɗan kamar fusace naji gyaran muryar MD a kaina. Saurin gyara yanayina nayi na maida hankalina gareshi, fuskarsa a ɗan ɗaure yana famar yamutsa fuska ya ce, “Ɗauka ki duba”. Ɗaukar nayi, sai dai ban kallaba yanzu na maida hankali garesa da nuna alamar shi nake saurare. Shima sai naga ya ɗan sassauta yanayinsa. Ya nuna ni da faɗin, “Samraah na zaɓoki ne saboda nasan zaki iya. Wannan mujalla ce ta TAURARINMU A YAU data fita jiya. A gaba ɗaya abinda ke cikinta ya ta'allaka ne akan matashin ɗan kasuwar nan da sunansa ke amsa kuwa a ƙasashenmu na Africa dama duniya a ɗan tsakanin nan. Wato *_AWWAB  EL-MU'AZZ._* sai dai kowa yafi saninsa da *_MAASH_* ne. Maash ɗan arewa ne haifaffen garin Kano sai dai mazaunin jihar Lagos. Yana da tarin cibiyoyin kasuwanci a kudancin ƙasar nan dama wasu ƙasashen Africa. Hakama a ƙasashen turawan da larabawa yana da rassan kasuwanci. Amma abin mamaki bai taɓa kafa wani abunsa a arewacin nan namu ba. Hakan yasa mutanenmu sukai masa ca, suke kuma sukarsa akan hakan, har takai suna ƙalubalantar dukiyar tasa musamman idan akai dubi da ƙarancin shekarunsa. Duk da kuwa an san mahaifinsa nada kuɗi, hakama Kakansa sanannen mutum ne, sai dai ko kwatar abinda shi MAASH ɗin ke da a yanzu mahaifinsa bai mallaka ba. Kace nace ya sake yawaita a kansa ne a watanni uku da suka gabata, dalilin bayyanar Companyn sa na jirage dake jigilar mutane daga Nigeria zuwa ƙasashen ƙetare. Domin a farko jirage goma ne ciff suka fara aiki. Sosai manyan gidajen jaridu sun so tattaunawa da shi amma Maash yaƙi bada kowacce irin dama. A duk lokacin da hakan ta taso sai dai a tattauna da P.A ɗinsa. To nadai taƙaice miki zance a yanzu haka bayan ka-ce-na-ce da aka sha yimasa akan gudun arewa da ƙaruwa Mujallar nan ta fitar da bayanan buɗe ɓoyayyen katafaren company da kusan wata uku kenan ana aikinsa batare da mutane sun san na wanene ba a cikin Kanon nan. Company ne na ƙera motoci da babura da abubuwa masu yawa da suka shafi ababen hawa. Irinsa shine na farko a Africa, a duniya kuma na uku. Kuma Maash da kansa zai zo Kano bikin buɗesa. Hakan yasa tunda naga mujallar nan na shiga na fita sai da na samo mana invetion card ɗin shiga wajen, dan hatta ƴan jaridar da zasu halarci wajen a ƙa'ide suke. Dan haka na kwana nazari a daren jiya, na kuma hanga na hango a kaf gidan nan kece nake ganin zaki iya mana wannan aikin, fatanmu kiyi duk yanda zakiyi kisa Maash ya magantu a gaban ƴan jarida karo na farko dan ALLAH. Hakan zai zama ba ƙaramar nasara ba a garemu da ma wannan gidan namu baki ɗaya. Sannan ke a karan kamki ma wata sabuwar ɗaukakace da nike da tabbacin zata zamewa rayuwarki alkairi in ALLAH ya yarda.”         Wani irin nauyi naji kaina yamun, dan haka da ƙyar na iya fisgo kalma ɗaya akan harshena na furta. “Amma Sir kaifa kace bai taɓa yarda yayi hira da ƴan jarida ba. Taya kake tunanin ni zan iya samo wannan nasarar? Yaushe ma na fara aiki, wane matsayi na taka a cikinsa? Ni wacece da zanyi abinda manyan ƴan jarida gogaggu suka gagara yi cikin sauƙi haka?”.        “Ba cikin sauƙi bane Samraah. Sannan al'amarin ba iyawa bace ko kaiwa wani matsayi. Sa'a ce kawai kuma kowa da irin tasa a rayuwa. Nima ba ina ji bane wai lallai sai hakan ta kasance ba. Fata dai nake yi da jin yaƙinin zaki iya in sha ALLAHU”.     Shiru kamar bazance komai ba, kafin kuma na sauke nannauyar ajiyar zuciya. Na ce, “Shike nan Sir zan gwada na gani, ai da gwaji jirgin sama ya tashi sama daga bisa ƙasa. Amma dai bani kaɗai ce zanje wajen ba?”.       Ƴar dariya yayi a karo na farko, cikin tsokana ya ce, “Kada kice min ke ɗin matsoraciya ce mana. Bayan kuma kallon jaruma nake miki. Kallabi a tsakanin rawuna”.     “Humm Sir bazaka gane ba. Irin waɗan nan mutanen da suke jin tamkar ma duniyar su suke mata alfarma ba itace ke musu na basu fili a cikinta ba suna kallon mutane ne tamkar wasu dodannin tsaffi a rayuwa. Dan a kullu yaumin zaka gansu ne zagaye da masu tsaro a kowacce kusurwa ta rayuwarsu. Ni gaskiya bana son ƙasƙanci koda a wajen wanda ya fini ne”.          “Wannan itace ɗabi'a ta cikakken mutum ai Samraah. Duk wanda yasan darajar kansa haka ake so kuma ya kasance. Kada ki damu bake kaɗai zaki je ba. Hasalima ke aikin ki shine gabatar da shirin kawai. Akwai Davido da Mansoor da Khulsoom a tare dake. Yanzu sai kije ki tsara tambayoyin da zaki masa ki kawo min, ki nutsu sosai wajen tsarasun daga nan har zuwa Monday, kinga kinada kwanaki kusan huɗu kenan tunda yau muna alhamis. Kije da wannan mujallar domin duba abinda suka rubuta a kansa. Za kuma ki iya wani binciken a kansa ɗin dai koda ta hanyar yanar gizo ne ko wasu mutane. Hakan da zakiyi ne zai baki damar tsara abinda ya dace a kansa ɗin, dan ina fatan mu zama mune taurarin mako mai zuwa”. Ya ƙare maganar yana murmushi.     Nima dai murmushin nayi, dan ya ba ni dariya. “In sha ALLAHU zanje nayi nazarin Sir. Maybe ma kafin Monday ɗin kaga na tura maka duk abinda na tsara ɗin koda ta WhatsApp ne”.          “Masha ALLAH, ALLAH ya bada ikon hakan. Amma dai baki da matsala kibi komai a sannu tunda nunada kusan kwana goma kafin ranar”.      “To nagode Sir”.   Na faɗa ina miƙewa hannuna ɗauke da Mujallar. Harna fice a office ɗin ina jin idanunsa a kaina. A raina nace (Maye kawai sai dai kaci kanka kasha baƙin ruwa).......✍️ _Tofa masu karatu yaya kuke tunani akan wannan aiki da MD ya damƙama Samraah. Shin zata samu damar haɗuwa da wannan matashi mai wahalar sha'ani mai suna *Maash* ko kuwa?_. _Idan ma ta haɗu da shi ɗin taya zata iya abinda wanda suka fita faɗa aji da gogewa akan irin aikinta suka kasa?_. _Shin wai wanene ma *Maash* ɗin nan ne? Minene dalilinsa na gudun yarda ya bayyana asalinsa ga ƴan jarida. Miyyasa yake ɓoye kansa? Minene baya son a sani game da shi ɗin?_ _Duka wannan amsoshin suna a kundin littafin TSUTSAR NAMA... masu iya magana sunce wai ITAMA ƊIN NAMA ce. Kuzo ku mallaki naku domin jin abinda littafin zai zo muku da shi, domin kuwa ƙumshe yake da abubuwa masu ban mamaki, al'ajabi, makirci, soyayya, cakwakiya, zamba cikin aminci, tare da ɗan karan munafunci daga ɓangarori daban-daban._ *_In sha ALLAHU sayen nagari maida kuɗi gida😊😉😉😘😘🫡🫡._* ______________ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑺𝒊𝒙_ .......Zaune na kai jagwaf a kujerar zamana ina dangwarar da mujallar da MD ya bani a desk ɗinmu. Mujallar Ruƙayya ta ɗauka tana faɗin, “Woow kaga wani handsome guy anan. Sam G daga ina haka? Waye shi?”.      Baki na ɗan taɓe kaɗan batare dana amsa mata ba na shiga ƙoƙarin kunna computer ɗin gabana. Itama batabi takan jiran amsar tawa ba ta shiga karanta abinda ke jiki. Wata ƴar zaburowa tai da zazzaro idanunta waje tana faɗin, “Kutt Sam-G wannan ai Maash ne.”    Duk ɗagowa sauran abokan aikinmu sukai suma suna kallonta. Sai kuma suka maido kallonsu gareni kamar yanda take kallona. Ganin na ɗauke kai tamkar bamma san mi sukeyi ba yasa suka sake maidawa kanta tare da miƙewa suka nufeta. Rufuwa sukai akan mujallar suna karantawa su duka huɗun, jin yanda duk suka nutsu yasa na ɗago na kallesu, batare da nace dasu komai ba na warce mujallar a hannun Ruƙayya. Ƴar harara na sakar musu ganin duk yanda suka ɗago suna kallona. “Malamai kowa ya koma kan aikinsa. Kun wani zauna karanta abinda bazai amfaneku ba.”      Ƴar dariya Usman da Asiya da Khalid sukai, yayinda Ruƙayya ta balla min harara. Magiya Usman ya shiga min yana faɗin, “Sam-G Please ki bamu mu ƙarasa karantawa, anya kinsan kuwa wanene wannan na jikin hoton?”.        “ALLAH bazan baku ba kuje kuyi aikinku, mi sanin nasa kuma zai amfaneni da shi da zan damu da so.”    Magiya suka shiga mun nace bafa zan basu ba, dole suka haƙura suka barni badan sun so ba. Sai dan ayyukan dake gabansu. Nima nawa aikin na cigaba dayi batare dana sake bi takan mujallar ba. Haka muka cigaba da aikin gabanmu har lokacin tashi yayi. Tarkacena na shiga haɗawa domin wucewa gida aɗan gaggauce, dan nasan Mansoor na jirana. A karo na farko idanuna suka sauka akan fuskar mutumin dake jikin mujallar lokacin da nake ɗakkota zan saka a jakka. Duk yanda naso kauda idanuna hakan ya gagara, dole nai tsai ina kallon ƙyaƙyƙyawar fuskarsa. Sam a zahirance baya kamanni da ƴan Nigeria ma bare Kano, duk da kuwa muma munada ƙyawawan fiye ma da kamarsa, sai dai kuma yanda hasken fatarsa yake tsaka tsaki dan bai wani yi haske dau ba zaka iya kiransa ko haif caste. Abu mafi ɗaukar hankali a fuskar tashi siririn baƙin gashin daya zagaye kumatunsa har zuwa haɓarsa ya kuma zagayo ta bakinsa ɗan ƙarami kamar ba namiji ba. Sam babu fara'a akan fuskar, sai hasken idanunsa dake a wani irin salo kamar na mai jin bacci. Abin mamaki tsakkiyar ƙwayarsu blue-blue zaiba-zaiba bansan yazan kirashi ba, ataƙaice kamar dai na mage ko masu jajayen kunne oho duk yanda kuka fassara. Sai cikakkiyar girarsa mai faɗi. Sosai na sake waro idanu lokacin da nakai dubana ga sumar kansa. Kitso ne guda huɗu akan nasa a kusan tsakkiyar kan dan ta gefe-gefe an aske sai saisayayyen sabon gashin daya kwanta luf-luf baƙi siɗik. Daga ta bayan kunnensa kam a dai-dai dokin wuyarsa zanen tattoo ne anyi fuskar zaki. Kunensa ɗaya manne da ɗan kunnen stone daketa wani irin sheƙi da ɗaukar ido kalar sky blue mai garai-garai kamar diamond. Wani wawan tsaki da ban san dalilin yinsa ba naja ina mai tura mujallar a bag ɗin. Dan sam nikam abin bai mun ba. Ɗan musulmi haihuwar arewacin Najeriya cikin Kano ne haka tamkar wani jinin yahudawa. Toni wannan tunda ma ba wani kama yake damu ɗin ba sosai ai gara ma a dinga jinginashi da ƙasashen ƙetaran mu bar musu kawai yafi, dan gaskiya aka bincika kam a cikin iyayensa akwai wanda ba bahaushe ba ko nace ma ɗan Nigeria gaba ɗaya. Da wannan mitar na fita a office ɗin, dan kusan ma nice ƙarshe su Khalid duk sun fice.       Horn da Mansoor yayi min ne ya ankarar dani in da yake, da alama dama ni yake jira, dan ina shiga yayma motar key muka fice. Har muka fita a layin da station ɗinmu yake muka hau titi sosai babu wanda yay magana a cikinmu. Sai zuwa can Mansoor ya katse shirun namu da faɗin, “Madam duk gajiyar ce haka?”.     Cikin ɗan yatsine fuska na ce, “Kawai dai”. Maimakon yaji haushi sai yay murmushi kawai, dan ya fahimci yau ɗin ƴan shiru-shirun ne a kaina. Dan ko ɗazu da muka haɗu dama bawani hira nayi sosai ba. Baiyi fushi ba ya cigaba da jana da hira, tun dai ina amsawa a sama-sama harna ware, dan akwai shaƙuwa mai ƙarfi tsakanina da Mansoor. Muna a gab da isa anguwarmu na takalo masa maganar da Uncle yay min akan aure kamar yanda Yaya Musaddiq ya bani shawarar nayi. Kamar wanda ya ɗan razana ya kallan, sai kuma ya maida hankalinsa ga titi da sauri ganin nima shi nake kallo..        “Lafiya kuwa? Naga kamar ka razana?”.       Murmushi ya saki tare da ɗan dubana, sai kuma ya gangara gefen titi ganin yanda duk na wani tsaresa da kallo. Sai da ya kashe motar da ƙyau ya juyo yana fuskantata. Ɗauke nawa idanun nayi daga kansa. Murmushi naji ya saki mai ɗan sauti, sai kuma ya fara magana a hankali. “Dole ne na razana ai Baby, dan farin ciki ne da yazo min a matuƙar bazata. Kema kin san tsahon lokacin dana ɓata ina fatan jin wannan furucin daga bakin ki. Taya yau na jisa ba zanji kaɗuwar farin ciki ba. Ki godema ALLAH ma da ban saki kan motar mun daki fitila ba. ALLAH na gode maka da ganin wannan rana a gareni, ni Mansoor zan mallaki TAURARUWAR MATAN DUNIYA”.       (🤥Ni dai banda ni eh🥱).   Murmushi ne ya suɓuce min, na kauda kaina gefe inayi duk da kuwa akwai facemask a fuskata, harma da eyeglasses dakan ƙara fiddo tsarin ƙyawuna a duk sanda na saka shi. Ganin murnar tashi bazata ƙare ba ga shi lokaci na tafiya murya can ƙasa-ƙasa na ce, “Please ka tada motar nan magrib fa zai yi”.          “A'a Madam, barni na gama murnata dan ALLAH. Mansoor ne fa zai mallaki Samraah Gwarzo. Wani shagalin ma ai sai naje gida hajjaju”.     “To nidai kaini gidan, idan kaje sai ka cigaba dayi”.     Da ƙyar na samu ya tada motar muka tafi, bakinsa baiyi shiru ba har muka ƙarasa. Nidai na sungumi bag ɗina na fice ina cemasa sai da safe.           A falo na iske duk mutanen gidan. Amma babu Hafizzullah da Abbas, da Nabel, hakama Abba da alama bai dawo ba shi da Yaya Musaddiq. Koda yake shi dama Yaya Musaddiq sai kai ma wata baka gansa zaune a falon nan ba. Iyaka ya shigo ya gaida Abba da dare, daga haka ya koma ɗakinsa, abincin gidan ma yakan daɗe yanzu bai cisa ba duk da nauyin kawowa ta dawo kansa badan kuma Abban ya rasa ba sai dan haka Mum ta tsara ayi. Mum ta watso min wata muguwar harara da ta sakani tura baki ta cikin mask ɗina. Batare dana sake kallonta ba nace “Mum good evening”.     “Ko kuma good uwarki ba”. Ta amsa a fusace. Dariya sosai Baby da Bibaa suka kwashe da shi. Sai autansu dake ta aikin homework ɗinsa kamar ma bai san abinda ake a falon ba. Tsawa ta daka min kan nazo.  A hankali na nufi gabanta na durƙusa, bamma gama kaiwa ƙasa ba naji saukar lafiyayyen mari daya nema gigitani, dan har eyeglasses ɗina sai da ya faɗi. Idanun kawai na rumtse da ƙarfi, sai dai naƙi yarda hawayen da suka ciko min ido su zubo. A fusace ta ce, “K dan uban uwarki har ni zan sakaki aiki ki tafi sabgar gabanki ki bar min?”.      Karo na farko na ɗan kalleta. Cikin danne kukan dake neman kufce min na ce, “Mum wlhy duk abinda kikace nayi ban tafi ba sai da nayi sa”.     “Oh ƙarya nake miki ke nan ko? Miyar da kika bari akan wuta uwarki ce tai fatalwa ta ƙarasa min?”.     Wani irin rumtse ido na sake yi ina cije lips. Babu abinda kemin ciwo a duniya sama da zagin iyayenmu da Mum kanyi. Kuma in har tayi hakan bana iya daurewa sai na mayar mata da murtani. Yanzun ma hakance ta kasance. Dan cikin kaushin murya da tsiwa na ce, “Mum ai kunsha tubarraki kenan, dan nasan duk abinda zai fito daga Ummie na mai albarka ne, to balle kuma ace fatalwarta, ai nasan albarkar sai ta ninka ma. Bara naje nai salla na sake mata addu'a dan gobe idan zatazo a fatalwar ta dafa mana har abincin ba ƙarasa miya kawai ba”.      Ba Mum ɗin ba hatta su Baby sagade sukai suna kallona. Nikam ko'a kwalar rigata na miƙe tsam. Batare dana yarda na kalla kowa a cikinsu ba na nufi hanyar ɗakinmu ni da su Bibaa, dan Baby tun muna yara tace bazata zauna dani a ɗaki ɗaya ba. Hakan yasa aka haɗani da Bibaa da auta. Nasha wahalar yaran sosai, dan dukkan nauyinsu kaina ya koma, ga fitsarin kwance. Dole nabar musu katifar na dawo kwana ƙasa saman tabarma. Bayan na fara zama budurwa nazata za'ace nabar cikin yaran na koma ɗakin Baby, amma shiru kake ji wai malam yaci shirwa. Sai ma wani sabon salon iskanci da ita Bibaa kan min yanzu, wai ita tana takura gaskiya a ɗakin dan munyi yawa. Ban taɓa cemata komai a kan hakan ba dai, dan fatana ma a yanzu Mansoor ya fito kawai ayi auren mu a wuce wajen. Shima Yaya Musaddiq yay nasa Hafizzullah ya koma gidansa ba shike nan ba mun bar musu gidansu........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑺𝒆𝒗𝒆𝒏_ .......Ina shiga ɗaki kukan da banyi ba a gabansu ya kufce min. Ban yarda nai zaman yinsa ba, na zame kayan jikina kawai na nufi bathroom. Tsayawa kawai nai ina kallon bayin raina a matuƙar ɓace. An masa kaca-kaca tamkar banyi wahalar gyaransa ba kafin na wuce. Nasan Bibaa ce tai masa haka. Dan tsabar iskanci har pad data cire guda biyu ta yasar a bayin da pants ɗinta. Inada ƙyanƙyami sosai a rayuwata, dan abu kaɗan ke ɗagamin hankali, shiyyasa ma nake bugar jikina na tsaftace gidan yanda ta kamata batare da jin ƙyashi ba. Hawaye tab da idona na shiga gyaran bayin, sai da na maidashi ƙal na tattara trash ɗin data tarama mutane na fitar. Har lokacin suna a falon zaune suna kallo har Mum ɗin, kai kace basu ji sallar magrib da akeyi ba. Na jima da fahimtar Mum saita gadama take salla, shiyyasa ƴaƴan nata ma dai gasu nan sai a hankali babu wanda ya damu da ibadar. A da Hafizzullah har ya fara ɗaukar ɗabi'ar, sai da na miƙe kansa ni da Yaya Musaddiq tamkar bama ƙaunarsa sannan. Sake zuwa nai na wucesu na koma ciki. Sai da nayi wanka na saka doguwar riga mara nauyi nai salla. Bayan na idar zaman yin karatun Alkur'ani nayi, ban ɗaga a wajen ba sai da akai isha'i, har lokacin kuma ina jiyo hayaniyarsu a falon, sallar dai bazasu tashi suyi ba. Falon na fito na wuce dan ɗaukar abinci na, amma sai na samu wayam. Banyi ƙasa a gwiwa ba na dawo ina tambayar Bibaa. Wani kallon banza yarinyar ta watsa min duk da kuwa na bata kusan shekara bakwai zuwa takwas, dan kwata-kwata yanzu take a shekara ta goma sha uku, a gadarance ta ce, “Kin bani ajiya ne. Ka jimin rainin wayo dan ALLAH mtsowww!!” ta maida kanta ta cigaba da abinda take yi. Bance komai ba na juya na koma ɗaki, dan hakan da tai na nufin yau banda abinci a gidan tunda na tafi aiki ban kammala miya ba, bayan kuma nayi komai har abinda ba'a sakani ba, miyar ma na barta ne kawai ta gama fidda mai dan karna makara tunda ta soyu. Wajen kwanciyata nakai zaune ina hawaye, dan haka kawai yau naji zafin abinda akai min ɗin duk da bawai yau ɗinne farko ba, amma kasancewar na dawo da yunwa sai abin ya zafeni. Tun muna yara idan Mum ta bushi iska takan hanamu abinci, haka Hafizzullah zaita kukan yunwa dan ni da Yaya Musaddiq mukan daure, ko zaiyi kukan mutuwa kuma bazata bashi ba sai dai Yaya Musaddiq ya fita ya samo masa a waje koda da bara ne, yanzu kam da muka girma idan aka hanamu zai sayo ya jamu ɗakinsa muci mu ƙoshi muna hirarmu. Sai kuma hakan ke ba Mum haushi take kai ƙararmu ga Abba wai muna haɗe kai muyita zaginta a ɗakin Yaya Musaddiq. Wani lokacin Abban kan mana faɗa, wataran kuma ya mata shiru, sai dai ta ƙaraci masifarta ita kaɗai. Ganin zaman bazai amfaneni da komai ba na miƙe ina share hawayena. Ƙaramin hijjab ɗina na zaman gida na ɗauka na saka, na ɗauki jakata dana fita aiki da ita na fito. Suna a falon har yanzu suna kallo, banko kalla kowa ba a cikinsu na fita zuwa ɗakin Yaya Musaddiq. Sai da na ƙwanƙwasa tare da yin sallama ya bani izinin shiga sannan na shiga. Tashi yay daga kwancen da yake a tabarmar barcinsa, dan koya sayi katifa amshewa Mum take ta bama su Bibaa su kasheta da fitsari ko a bama su Abbas. Kusan sau uku tana yin hakan shiyyasa ma ya bar saya shima. Murmushi yay min yana mai bina da kallo, na ɗan tura baki gaba ina zama a gefensa da ajiye jakar kamar a yanayin gajiye. Yaya Musaddiq mutum ne mai sauƙin kai sosai, da wahala ka iya ganin fushinsa a zahiri. Cike da kulawa ya ce, “Kandala miya faru kuma ake kumbura wannan cat face ɗin?”.       Sake tura bakin nayi da faɗin, “Ni ba komai, yunwa nake ji”.    Ɗan jimm yay yana kallona, sai kuma ya ɗauke kansa da sauke ajiyar zuciya ya miƙe. Rigarsa ya ɗauka ya saka a saman singlate ɗin jikinsa. “Ki jirani ina zuwa”.       Kaina na jinjina masa ina kaiwa kwance a tabarmar tasa. Yana fita na ɗan lumshe idona. Kusan minti huɗu ina a haka sai kuma na miƙe zaune. Jakar tawa na jawo gabana, tare da zuge zip na ciro mujallar nan da MD ya bani ɗazun. Yanzu kam kai tsaye na zubama mujallar ido, sosai nama mutumin kallon ƙurilla a karo na biyu, badan baiyi haske dau irin na larabawa da indiyawa ba da tabbas zan iya cewa daga cikinsu ya fito. Dan daga suffar jiki har zuwa ta halitta fuska bai yi kama da ƴan Nigeria ba. Sai dai kuma abin mamaki fatarsa zamu iya cewa irin tamu ce. Duk da kuwa ba baƙi bane wulik, idan ma za'a kira farare za'a iya nunashi mu anan Africa, sai dai kuma farin nashi yasha banban, koda yake maybe camara ce ta maida shi hakan. Sake maida idanuna akan kitson kansa dake ɗaure a tsakkiyar kai kamar wani mace, sai kawai naja sirrin tsaki, banda ƙarshen duniya dai ace namiji da kitso da ɗan kunne. Kai ALLAH ya ƙyauta, inaga dai ɗan daudu ne gaskiya. Dangwarar da mujallar nayi gefe na sake komawa nai kwanciyata. A dai-dai nan Yaya Musaddiq ya shigo ɗakin da sallama. Amsa masa nai ina tashi zaune. Ya ajiye min ledar hannunsa yana faɗin, “Oya tashi kici”.     Babu musu na tashi zaune, ina ƙoƙarin buɗe ledar shima yana kaiwa zaune ya ɗauki mujallar. “Tofa! Ke kuma ina kika samo _Maash_ haka kandala?”.        Baki na taɓe da fara kai lokar indomie ɗina. Kafin na ce, “MD ɗinmu ne ya bani yau wai zanyi aiki a kansa”.      “Aiki kuma?”.   “Eh Yaya, so suke wai nayi hira da shi a ranar bikin buɗe Companyn sa”.   “Kai lallai sun haɗaki da aiki. Amma ALLAH ya bada nasara”.       “Amin” na amsa masa ina sake jin karaya. Sai kuma na kallesa, batare da nasan ya akai bakina ya suɓuce ba na ce, “Yaya amma dai shi ba musulmi bane ba ko? Sannan ba ɗan Nigeria bane?”.       Sosai ya waro idanu waje da faɗin, “Kai! K waye ya gaya miki ba musulmi bane?”.     “To Yaya wane musulmi ne zai zauna ai masa kitso a saman kai ya ɗaure haka kamar wani mace. Ga ɗan kunne kuma a kunne ga tattoo a wuyansa. Sannan kalli idonsa kamar na mage fa. Ni wlhy banji ya birgeni ba abu kamar ɗan daudu”.       Dariya Yaya Musaddiq ya saki yana girgiza kansa. Ya ce, “Banda abinki Samraah dan mutum yayi duk wannan sai a fiddashi a musulunci ko a kirashi ɗan daudu. Wannan abun da kika gani yanzu shine samari suka ɗauka matsayin gayu da wayewa wai, baki ganin kuma shi ɗin mai lokaci ne da duniya ke ji da gani. Idan kuɗi na ɗibar mutum ai komai ma sai ya yi ba komai bane. Sannan shi ɗin kamar ance ruwa biyu ne. Tsakanin kakansa da kakarsa akwai wadda ba ɗan Nigeria ba, anan ma ya kwaso waɗan nan kamannin da kowa ke ganin ba ɗan 9ja ɗin bane ba. Amma asalin mahaifinsa ɗan kwanar Mashi ne ma, Kinga kuwa shi cikakken bakano ne, anan ma aka haifesa shi”.      Baki na taɓe akan maganar yaya ta kusan ƙarshe, sai kuma na ce, “Humm, to ALLAH ya rabamu da irin wannan kuɗin masu mantar da bawa shi waye kuwa. Ni yanzu Yaya yaya zanyi to. Wlhy duk kaina ya gama kullewa fa?”. “Karki damu in sha ALLAHU zamu samo mafita. Ke dai kawai ki saka a zuciyarki zaki iya. In dai shi ba aljani bane nasan duk taurin kan Maash bazai gagari Kandalata ba ai. Dan itama tauriƙiƙin kantace ga naci akan abinda tasa gaba”. Dariya na ƙyalƙyale da shi da faɗin “Kai yaya?” Ya ce, “ALLAH ai nasanki ne fiye da yunwar cikina kandala”. Nanma dariyar nayi shima yana tayani, tuni Yaya ya mantar dani baƙin halin mutanen gidanmu. Ya kuma bani ƙwarin gwiwa sosai data bani karsashi akan tunkarar wannan aiki da MD ya bani, ban baro ɗakin ba sai da na fara hammar barci.... Washe gari ban ɗaga ko tsinke ba a gidan, dan banma tashi a barci ba sai ƙarfe bakwai. Salla nayi nai wanka nai shirin office nai tafiyata, dan har lokacin babu wanda ya tashi suna can suna barci ana jiran jaka ta gama girkawa a fito a ci. To ai na fisu iya tsiya, dan kamar yanda na saba in har aka gunziga min baƙin ciki a gidan sai na maida murtani. Yaya Musaddiq bai san tsiyar dana shuka ba ya ɗaukeni muka wuce a mashin ɗinsa. A hanya nake roƙonsa wannan weekend ɗin muje muga Hafizzullah a Katsina dan ALLAH idan baida aiki da yawa. Bai musa ba yace min in sha ALLAHU zamuje ranar asabar sai mu dawo lahadi. Sosai naji farin ciki, harma na manta da damuwata balle na sanar masa banyi breakfast ba na gudo yau. Yana sauke ni ya miƙamin 1500. Amsa nayi ina masa godiya da yima iyayenmu addu'ar samun rahama. Daga haka na shige shi kuma ya wuce.          Kasancewar yau inada gabatar da program banfi zaman mintina talatin ba na tashi na fita tare Khalid. Kusan cin karo mukai da Mansoor dake ƙoƙarin fitowa. Baya naja da sauri, sai hakan ya sakani tuzguɗewa na tafi zan faɗi. Kusan tare suka kawo hannu shi da Khalid domin taimaka min, niko nai saurin sake maida jikina baya ta yanda kowannensu bai samu damar taɓanin ba, dan na gwammaci na faɗin kawai. Aiko faɗuwar nayi, na kuma ji zafi sosai, duk da kuwa na fuske Mansoor sai da ya fahimci hakan. Cike da damuwa yakai duƙe gabana tare da sake kai hannu zai riƙo nawa na ɗan hararesa. Murmushi kawai yay ya janye hannunsa yana kaisa saman kansa ya shafa cike da basarwa. Sai kuma ya sake maida idonsa gareni, a hankali ya ce, “Yanzu har kina da damar yin masifa babie. Naga dai hannun ai nawa ne”.      Sake hararsa nayi tare da ɗauke kai ina ɗan murguɗa baki, na ce, “Sai ka bari sai ka biya ai”. Ina kai ƙarshen maganar na miƙe abina. Dariya ya saki mai sauti da faɗin, “Rigimammiya kawai ai saura ƙiris dai, mi kike ci na baka na zuba. Wata uku bazaki ƙaraba sai da igiya uku na ciff a kanki”.          Murmushi kawai nayi ina ɗan murguɗa bakina dake cikin face mask ɗina na wuce na barsu a wajen Khalid na tayasa dariya. Sai da na gaishe da kowa kafin na wuce na ɗan ƙara gyara fuskata gaban mirror, suma su Mansoor sun shigo, dama mu zaije kira ashe. Hakama baƙonmu na yau ya iso tuni, dan haka babu ɓata lokaci aka fara gabatar da program ɗin........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑬𝒊𝒈𝒉𝒕_ .......Yau ma kamar kullum Mansoor ne ya ɗaukeni zuwa gida bayan an tashi. Mun ɗan fara tafiya nake sanar masa aikin da MD ya saka ni. Da mamaki ya juyo yana kallona da faɗin, “What! Dama ke ya bama aikin nan? Taya zai haɗaki da wannan aikin mai wuya bayan yasan wanene wannan mutumin. A tarihinsa fa bai taɓa yarda yayi hira da ɗan jarida ba har yanzu. Kuma karki ɗauka wai ƴan jaridar nan gida Nigeria kawai. A'a har manya-manyan ma irinsu BBC, VOA, Aljazeera da ire-iren su. A duk sanda aka buƙaci hira da shi sai ya haɗa mutane da P.A ɗinsa...”         “Hu'umm, to amma shi miyyasa yake yin haka? Kamar ba wayayye ba? Ko kuma bashi da gaskiya ne shiyyasa yake gudun hakan?”.      “To ALLAH kaɗai masanin gaibu, sai kuma shi da ya barma kansa sanin dalilin. Amma dai wasu na ganin girman kai ne kawai da giyar kuɗi dake ɗibarsa. Dan a yanzu fa shine matashi ɗan kasuwa na biyu a duniya dake juya manyan kuɗaɗe, anama hasashen nanda shekara mai zuwa zai iya zama na farko. Wasu kuma na ganin akwai dai wani babban dalili nashi, dan in har da girman kai ne ai zaiso ƙara bayyanama duniya shi ɗin wanene ta hanyar ƴan media ɗin. Wasu ko na ganin ko dodon tsafinsa ne yace kar yay hakan, kin san dai mafi yawan ƴan kwasuwar nan dake shahara a ƙanƙanin lokaci sai a hankali, shiyyasa ake yawan ɗora musu zargi, ALLAH dai masanin gaibu. Amma gaskiya al'marin dai nasa akwai ɗaure kai”.         “Ƙila to aljanu ne da shi da basa son hira da ƴan jaridar. Ko kuma dai da gasken dodon tsafinne da shi. Dan ni naga yanda kowa ke misalta dukiyar tasa akwai ban tsoro kam”. Na faɗa cikin halin ko in kula. Dariya sosai Mansoor ya sanya, tare da faɗin, “Kai Babie baƙya rabo da wauta ALLAH. Aljanu kuma? Namiji da aljanu? Adai tsaya a dodon tsafin”.     “To inba aljanu ba shi kam ai abin nasa yayi yawa, dodon tsafin ma kuma ai aljanu ne. Yanda yake nuna kansa a matsayin wayayye irin haka ai ya kamata ace an wuce wannan ajin. Amma ni kam in sha ALLAHU sai na sakashi ya magantu, ni halin nasa ma sai ya ƙara min ƙwarin gwiwar tunkararsa.”        Sosai Mansoor ya juyo ya kalleni cikin nuna mamakinsa a fili. Sai kuma ya maida kansa ga titi yana faɗin, “Anya yarinyar nan kin san wanene *_MASH!?_* kuwa? Babu sauƙi fa a ɗaukar wannan alwashin naki. Ni dai ina gargaɗarki da kar kiyi wani abu mara ƙyau dan ALLAH. Idan kin samu dama kamar yanda kowa ke fata fine, idan baki samu ba ba faɗuwa bace. Dan haka be careful sweetie. Kar ki biye ta MD kujerarsa kawai yake yunƙurin saitawa”.         “Karka damu, ni ba wani abu mara ƙyau zanyiba ALLAH. Kuma duk ma tambayar da zan masa ai sai na kaima MD ɗin ya duba. Kaima kuma zan baka ka gani kafin ma na turama MD ɗin har ma Yaya Musaddiq. Kawai dai ina fatan karya masa wannan alfaharin nasa ne”.        Kansa ya jin jina min, ya ce, “To ALLAH ya bamu sa'a, dan zanfi kowa kasancewa a farin ciki ace kece kika karya ɗin kam. Dan har ƙyauta sai na miki na musamman”.     “Tami?”.   “A'a ai ba sai na faɗa ba. Yanzu dai ajiye ma wannan batun. Su Alhajina fa zasu zo wannan weekend ɗin. Dan haka yau ina buƙatar ganawa da Abba yaya za'ayi kenan”.        Da sauri na juyo na kallesa, ya jinjina min kai alamar tabbatarwa. Kaina na ɗauke cikin jin kunya, sai dai wani irin farin ciki ne ke ratsa ƙashina da ɓargo har ina jin yanda jikin nawa ke rawa. Amma dai nayi juriyar dakewa. Sai dai ban sake cemasa komai ba har muka iso. Tunda ya tsayar da motar na kasa wani motsi, mun kai minti biyu a haka shi kuma yana kallona kamar ya samu tv kafin ya saki ɗan murmushi mai sauti. “Wai kunyar ce dai Babie?”. Sake kauda kaina nayi gefe batare dana bashi amsa ba. Ya saki ƴar siririyar dariya yana ɗan dukar sitiyari, sai kuma ya juyo gareni yana faɗin, “ALLAH ya kaini randa zan cire wannan kunya dai kowa ya huta, dan bazanyi sakaci ba a daren farko zata kama gabanta. Anya baki haɗa jini da fulani ba Samraah”.        Hannu na kai ga handle ɗin ƙofar zan buɗe na gudu sai na jita gam alamar ya saka lock. Kasa sake wani yunƙuri nayi, na kuma kasa juyowa dan har lokacin ina jin kallon ƙurullar da yake min.    “Kayi haƙuri ka buɗemin, zancen ganin Abba kuma ya kamata ka fara ganin Yaya Musaddiq dai first nake ga”.         Sosai ya sauke numfashi mai nauyi, sai kuma ya amsa da, “Okay hakan ma yayi, zan bari to sai gobe in sha ALLAHU na samu Yaya a gareji”. Daga haka ya buɗe min. Wuff na fice abina kuwa. Batare da ko sallama nayi masa yau ba na shige gida, har lokacin kuma ina jin idanunsa a kaina. Ina rufe ƙofar gate ɗin na jingina a jiki ina sauke numfashi, sai kuma na kai hannuna saman ƙirjina da ke bugawa da sauri-sauri. Murmushi na saki kafin na buɗe idanuna a hankali na ɗan leƙa gate ɗin naga ko ya wuce. Sai lokacin naga yana ƙoƙarin yin reverse. Bazan ɓoye miki ba ina matuƙar ƙaunar Mansoor wlhy Bilyn Abdull, soyayya nake masa mai ƙarfin gaske da bama zan iya misaltata ba, dan Mansoor ya mun abubuwa na halacci da dama akan soyayya da bazasu iya ƙirgiguwa ba, na tabbata da aure kawai zan iya masa godiya a kansu amma bada fatar baki ko soyayyar saman titi ba.              Cikin gidan na shiga kamar yanda na saba, sai dai acan ƙasan raina ina ɗan jin tsoro-tsoro. Sosai na sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi ganin ban samu kowa a falo ba yau. Zuruf na shige ɗakinmu, in da na tarar da Bibaa kawai tana kallo a wayarta. Yanda bata amsa ko sallamata ba nima ban sake bi takanta ba. Wanka na farayi duk da kuwa cikin ƙyanƙyamin bayin nai haka, dan yanda ban wanke ba haka Bibaa itama bata wanke ba, sai ma datti da suka ƙara masa. Gudun kar lokacin sallah ya wuce min yasa ni saka doguwar riga kawai na saka hijjab na tada sallar. Na kai raka'a ta biyu ina sujidar ƙarshe kawai naji saukar duka kaina. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un wata irin azabace ta ratsa ni, amma na daure sosai na cigaba da sallata. Abinda kuma zai baki mamaki ba'a daina dukan nawa ba har na idar. Karo na farko kenan dana ɗaga hannu sama ina kuka da neman sakayya wajen UBANGIJI na, ina ƙoƙarin shafa addu'ar dai dai nan Abba ya shigo kamar wanda aka jeho.        “Haba Jalilah minene haka? Baki da hankali ne tana salla kina dukanta”. Ya faɗa a matuƙar hasale yana riƙe bulalar. Basu ba hatta ni sai da na shiga shock, dan nidai nasan ba yau ne karan farko da Mum take dukana ba a gidan nan. Hasalima ta dakeni a gabansa a lokuta barkatai amma bai taɓa cewa komai ba. Bama ni ba, hatta da Yaya Musaddiq yasha shan duka a wajen Mum, yanzu ne dai ta daina sai zaginsa da baƙar magana. Hakama Hafizzullah, sai dai duk ni na fisu shan wahala kasancewar akoda yaushe ni ina cikin gida a tare da su....         Mum ce ta katse min tunani na, dan cikin hargagi ta hayayyaƙo ma Abba a gabanmu. Idan ni bazata ji nauyina ba ai ya kamata taji nauyin su Babie kasancewar sa na mahaifinsu. Amma ko'a kwalar kwagirinta. Dan sai da takai ya koma bata haƙuri da lallashinta. Ni al'amarin nasu ma sai ya nema fasan kaina dan al'ajabi. Haka dai ya jata da ƙyar suka fice a ɗakin. Harara Baby ta watsa min da faɗin, “Shegiya mayya. To kurwar iyayenmu kur wlhy. Kuma indai Mum ce kaɗan ma ta miki wlhy, bari dai Abban ya fita duk da ma ko yana nan zata iya cigaba da cin ubanki, yanzu ɗin ma ta ƙyaleki ne kawai kiji da wannan tsamin jikin mtsowww makwaɗaitan banza da wofi anzo an cika mana gida an hanamu rawar gaban hantsi”. Daga haka ta fice kamar iska zata ɗibeta. Dan sam Baby bata da wani jikin kirki, ta girman amma na fita cikar halittar jiki sosai, wanda ma bai sani ba sai ya ɗauka nice babbarta. Sai da suka gama zageni tsaf ita da Bibaa suka fita sannan na fashe da kuka, dan illahirin jikina raɗaɗi yake min sosai. Da ƙyar na iya tashi na zare hijjab ɗina, abinka da farar fata wasu wajen ma har sun fashe. Cikin ƙanƙanin lokaci zazzaɓi mai zafi ya rufeni, haka na kwana ina makyarkyata ga ciwon jiki. Duk kiran da Yaya kemin a waya ban ɗaga ba, har ya gaji ya daina kiran, nasan dai ya zata ko barci nayi ne...        Humm wato Bily inada taurin kai fiye da yanda kike tunani. Zaki sha mamaki idan nace miki washe gari ma duk da dukan da naci haka na sake tsallakewa nai tafiyata wajen aiki batare dana ɗaga ko tsinke a gidan ba. Nasan dai nabar ƙura sosai, amma ko'a jikina nai gaba batare da na jira ko Yaya Musaddiq ba yau. Sai wajen 12 sai gashi yazo lokacin ina kwance zazzaɓi ya addabamin. Ruƙayya ce data lura da haka ta matsa min nasha paracetamol da ƙyar. Da Yaya Musaddiq ma yazo itace tazo ta kirani dan ta ɗan fita taci karo da shi shine tazo ta kamani muka fita.      Kallo ɗaya na masa na duƙar da kaina. Dan sosai naga ɓacin rai tattare da shi. Sai dai shima yanayin da ya ganni naga ya ɗan raunana fushin nasa, dan muna isowa inda yake sosai naji ya sauke ajiyar zuciya yana mai furzar da huci mai zafi.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑵𝒊𝒏𝒆_ ........Sai da Yaya yayma Ruƙayya dake shirin barin wajen godiya sannan ya juyo gareni. Kallo ya ƙare min daga sama har ƙasa sannan cikin yanayin fusata ya ce, “Miyasa kike da taurin kai ne wai Samraah?. Yanzu ga abinda kikayi jiyan wace riba kikaci tunda kinfi kowa sanin halin matar nan?. Amma ke da yake ba'a taɓa faɗa miki kiji shine yau ma kika kuma. To ai gashi nan ta sake ƙulla miki sharri kala-kala ita da yaranta. Tun ɗazu ina gidan basu barni na fito ba sunata min masifa akan wai ni nake sakaki. Har Abban na saka sharaɗin ko dai ki ajiye aiki ki dawo ki cigaba da aikin gidan ko kuma ya aurar da ke ga wa wanda ita Mum ɗin ta kawo. Idan yaga shi zai barki yin aiki ki cigaba, amma albashinki dolene kema ki dinga rabawa biyu daga yanzu kina basu rabi ana haɗawa ayi cefane. Nama kawo masa batun Mansoor yaƙi ya saurareni sam. Wai shi bai san da wani Mansoor ba kuma bazai aura masa ke ba, wanda Mum ta kawo kawai ya sani kuma shi zai bawa dan yaron nada tarbiyya sosai, kuma shi ya gamsu da hakayensa....”       Kuka na sakar masa mai taɓa zuciya. Hakan ya sakashi yin shiru ya gagara cigaba da magana ya zubamin ido kawai. Kusan mintuna uku ina kukan sosai kafin ya kai zaune kusa dani. A jikinsa ta gefe ya sakani kawai shima hawayen na cika masa ido. “Amma kin san bana son kuka ko Samraah”. Ya faɗa muryarsa na rawa. Ɗagowa nai a karo na farko ina kallonsa. Sai kuma na sake fashewa da wani sabon kukan ganin yanda idanunsa suka kaɗa sukai jazur gasu cike da hawaye. “Yaya ya kake so nayi, shike nan haka zamu lalace a yima waɗanda basu taɓa jin tausayinmu ba biyayya. Kullum burin matar nan wulaƙanta mu, Yaya tun fa ban isa iya aiki ba nake bautar gidan nan, amma ko sau ɗaya ba'a taɓa min adalci ba idan nai kuskure a yafe min. Kullum kuma a banayi nake. Su Baby na kwance. Yaya na gaji wlhy, ji nake kamar na gudu na bar gidan nan kawai....”         “Shiii!!! Karna sake jin irin wannan maganar a bakin ki. Samraah ai wuya bata kisa. Da ace tana yi wlhy da bamu kai haka a rayuwa ba. Duk can baya baki ƙosa ba sai yanzu da aski yazo gaban goshi. Kwana nawa ma ya rage miki a gidan. Bama ke ba da kike mace zaki tafi gidan aure hatta ni da Hafizzullah in sha ALLAHU mun kusa bar musu gidansu. Gara kawai na tada gini na kamar yanda kike bada shawara mu koma can kawai. Amma dan ALLAH ina roƙonki kada ki sake maimaita abinda kika faɗa yanzu. idan kin gudu ina zaki? Ki daure ki cigaba da musu abinda suke so. Watarana sai labari ai. Maganarki kuma da Mansoor na yanke shawarar zuwa wajen dangin mahaifinmu, duk da sun watsar damu basu taɓa waiwayen mu ba tunda ɗan uwansu yabar duniya zanje na roƙesu su shiga wannan maganar a baki wanda kike so tunda dama sune ai da wannan alhakin ba Abba ɗin ba. Ki tashi kuma muje asibiti dan jikinki akwai zazzaɓi sosai.”        Ɗagowa nai zanyi magana ya girgiza min kai alamar kar nace komai. Dole na haɗiye kuwa. Ruƙayya ya kira da wayata, yace ta tattare masa kayana dan ALLAH. Cikin mintuna kaɗan ko sai gata. Da taimakonta muka fita inda mashin ɗinsa yake. Ta taimaka min na hau muka wuce dan Mansoor yau baizo office ba sunje wani aiki Jigawa. Sai da muka fara tsayawa a camix aka dubani kafin mu ƙarasa gida dan nata roƙonsa kan bazanje asibiti ba, sanin da yay min na ƙin jinin asibitin shima yasa ya barnin mukaje camix ɗin kawai aka bani magani.       Kamar yanda Mum ta shirya cin ubana shima Abba ya shirya hakan yau, sai dai a yanayin da Yaya ya shiga dani gidan ya saka jikinsa yin sanyi shi. Dan Mum ta fara min tujara da ƙoƙarin kai mari ya dakatar da ita.    “Uhm Jalilah inaga ya kamata ayi hakuri ai, baki kula da halin da take a ciki bane? Kiyi haƙuri harta warke ni da kaina zan sauke mata taurin kan nan nata nayi miki alƙawari”.      Wani shegen kallo ta watsa masa a fusace. Kamar zatayi magana sai kuma mita tuna oho tai shiru. Fuuu ta wuce bedroom ɗinta ta barmu tana faman huci. Wannan zazzaɓi dai shine ya ceceni a wannan rana. Washe gari kuwa duk da weekend ne asubar fari Mum tazo ta tadani. Bata damu da yanayina na har lokacin ban gama dawowa dai-dai ba. Nima sai bance mata komai ba na tashi na hau aikin da take buƙata, dan kwana biyun nan fa da banyi komai ba haka gidan yake zaune kaca-kaca. Kafin takwas na safe har brackfast na kammala haɗawa, na ɗauki na Yaya Musaddiq na kai masa. Na samu ya kammala shirin wucewa Gwarzo kamar yanda ya faɗa zaije. Ba haka naso ba, dan naso ace munje munga Hafizzullah kamar yanda muka tsara. Zama nai muka karya tare yana ƙara lallashina da mun nasiha, jinsa kawai nakeyi, dan gaskiya bazan iya haƙurin wani abun ba in har nayi wani. Amma dai zan rage taurin kan kodan shi. Ban bar ɗakin ba sai da ya ƙarasa shiryawa muka fito tare, yau zai dawo, amma ya musu tsaraba. Ciki na koma na samu mutanen gidan gaba ɗaya a falo zagaye da Abba. Sai dining dake kaca-kaca sun gama karyawa amma babu wanda ya iya kawar da ko cokali. Abban na gaisar, ya amsa min babu yabo babu fallasa, itako Mum bama ta amsani ba. Ban damu ba dan ba yau na fara ganin hakan ba ai daga garesu, na nufi ɗaki da nufin yin shirin islamiyya da nake zuwa duk weekend Mum ta dakamin tsawa.        “K dan ubanki waye zai kwashe miki waɗan can kayan”.     Ɗan jimm nayi a tsaye zuciyar na yunƙurowa, sai dai nasihar Yaya Musaddiq dana tuna ta sakani komawa cool. Batare da nace mata komai ba na nufi dining ɗin na shiga tattare kayan. Sauri-sauri na wankesu na fito, har yanzu suna a falon, ɗaki nai wucewata na shirya, na sake fitowa dai na samesu. Da harar Mum na fara cin karo, ɗauke kaina nayi kamar ban ganta ba, a ladabce naje gaban Abba na duƙa. “Abba zanje islamiyya saina dawo”.         Kansa kawai ya jin jina min ya cigaba da kallonsa. Nima sai na miƙe. Mum dake watsamin hararace tai saurin faɗin, “Ya kake bata damar tafiya Abban Abbas, idan ta tafi ubanwa zai mana girkin rana? Islamiyya take zuwa ne ba yawon iskancinta ba”.      Ƙoƙarin ficewa nake da sauri dan nasan zai iya dakatar dani. Amma a mamakina sai naji yana faɗin, “Baga su Baby nan a gidan ba suyi girkin su mana tunda sun ɓarar da tasu islamiyyar su....” daga haka ban ƙarasa jin abinda yake faɗaba nai wucewata ina murmushi. Wani lokacin idan Abban yay abu sai kaga kamar mai mutunci. Koda yake dama ba laifinsa bane ba, zama kawai ake ana shirya mana sharri a wajensa maybe ma harda asiri. Dan nikan ban taɓa ganin mijin dake tsoron ɓacin ran matarsa irin Abba ba. Oho koma dai minene su suka sani ina ruwana.. Tunda na isa islamiyya na samu ƙawayena biyu na manta da wata hidimar gidanmu. Sai ƙarfe huɗu muka tashi, anan nai sallar la'asar sannan na dawo gida. Abin dariya abin takaici, a galabaice na samesu wai babu wanda ya tashi yay girkin ana jirana, Abba dai ya fice sai su kawai. Sai Abbas dana samu a gidan shima ya shigo. Ko kallon inda yake banyi ba dan ni da shi bama magana. Haka na tuɓe uniform ɗina na shiga kitchen ɗaura musu girkin da suke jira ɗin. Abu mai sauƙi na musu nayi komawata ɗaki..        Yaya Musaddiq bai dawo a ranar ba kamar yanda yace. Koda na kirashi a waya sai yace nai haƙuri bai samu kawu Musa bane a gida, su kawu Sa'adu kuma sunce dole ya jirashi. Mun ɗan yi hira mukai sallama saboda kiran da Mansoor keta faman yimin. Hira sosai mukasha da Mansoor, dan sai kusan ɗaya mukai sallama. A hakan ma ba kwanciyar nayi ba. Tambayoyin da zanma wancan mutumin nai zaman tsarawa, har biyu sannan na miƙe na gyarama su Bibaa rufa na ɗauro alwala. Nice ban kwanta ba dai sai kusan biyu da rabi, amma hakan bai hanani tashi da asuba ba yin ayyukana.             Washe gari da yamma Yaya Musaddiq ya dawo gidan. Na dawo daga aikan da Mum tamun rijiyar lemo wajen ƙawarta na samu ya dawo. Naji daɗi sosai, dan bamma shiga gidan kai aikar ba na zauna muka hau hira. Duk yanda sukai da su Kawu Musa ya sanar min. Sunyi faɗa sosai, da farko ma ca sukai su babu ruwansu. Shi Abban daya nuna musu shine dolenmu yaje ya aurar damu. Amma Yayan ya dinga basu haƙuru, da ƙyar dai suka haƙura, sun kuma tsaida shi kawu Sa'adu zai zo ya sami Abban. Hakan kuwa akai, dan washe gari Litinin sai ga kawu Sa'adu. Lokacin mu duk mun fice wajen sabgoginmu. Shima Abban a office kawun ya samesa suka tattauna. Duk da dai a farko taso tayi tsami a tsakaninsu. Kasancewar kowanne yana son nuna ƙarfin ikonsa a kammu da kuskuren da ɗan uwansa yay masa. Bayan dai sunyi sama sun faɗo suka dai-daita kansu. In da da ƙyar Abba ya amince da batun Mansoor........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒆𝒏_ .......Oho mu bama musan sunayi ba, dan lokacin da suke nasu bidiri ni inama can office ɗin MD na kai masa aikin daya saka ni. Kamar kullum yau ma a kwai mask a fuskata, sannan dogon hijjabi ne har yana jan ƙasa na saka. Dama dai shigar tawa kenan. Idan har ka ganni babu hijjab to abaya ce na saka kuwa. Amma gyale dai a jikina zan iya rantsuwar tunda ma mallaki hankalina na san kaina ban taɓa sakawa ba. To bamma da shi sam, sai ƴan madaidaita da nakanyi rolling idan zan saka abaya. Duk da yanda na suturta jikina bai hana MD zuramin idanu ba, dan shi indai kallone ya iya shi na masifa ma da UBANGIJI ya hanemu yi. Ni dai miƙa masa takardar nayi na maida hankalina akan wayata.        “Wow! Kai Samraah sannu da ƙoƙari. Shiyyasa duk girman gidan nan ke na fara hangowa dan nasan bazanyi zaɓen tumin dare ba, saboda nai matuƙar yarda da basirar ki, kina da saurin ɗaukar abu wlhy. Sosai komai yayi, sai fatan ALLAH ya kaimu ranar kuma. Yanzu zuwa anjima sai kizo ki amsa kiyi printing nashi ko. Ki kuma je ki zama cikin shiri na musamman, dan wannan ranar muna fata ta zama ta musamman a garemu. Dan ALLAH kada ki saka dogon hijjabin nan tamkar matar limamin anguwa. Ki yi shiga ta ƴammatan zamani dan kin san irin manyan mutanen nan sunfi son komai na wayewa su balle shi matashi dake a ganiyar samartaka. Inda son samu ne ma ki saka sabbin kaya, ki samu makeup artist ta tsantsara miki irin kwalliyar nan taku ta zamani Please”.        Yanda kuka san television haka nai galala ina kallonsa. To amma kun san tsiyar mutuniyar taku. Sai ban musa masa ba nayi murmushi kawai da faɗin, “In sha ALLAHU Sir”. Yako ji daɗi, dan tuni ya washe baki da jera min godiya. Niko sai nayi dariya kawai a raina. Kuga ɗan banza yana son iskantani kawai. Yo in ba son iskantawa ba taya zai ce nai irin wannan shiri dan kawai burge wani sakarai can da ban san ma a wace alƙibla yake ba, ta musulinci ko ta masu kaɗa ganguna. Humyim bai san halin ƴar Abdul-wahab ba ne ba, amma zan sanar da shi sannu a hankali. Office na koma na cigaba da harkokina. Bayan azhar kuma muka haɗu da Mansoor. Dan nifa da kuke gani na duk rintsi bazaka ganni office ɗinsa ba in ba a dalilin aiki ba. Dan tun farko daya fara nuna buƙatar hakan ta hanyar kirana wai nazo na samesa office na dakatar da hakan. Nama nuna masa anan fa aiki mukazo, ya kamata mu ajiye batun alaƙa gefe muyi abinda ke a gabanmu kamar yanda muka rayu a makaranta. Idan mun fita anan sai mu dawo da batun alaƙar. Mansoor mutum ne mai sauƙin kai da fahimtar abubuwa, sai in kana kallonsa daga nesa ne zaka fassarashi da girman kai. Ya fahimceni harma ya nuna jin daɗinsa da hakan. Bawai dan ina zarginsa da wani mugun haline nayi hakan ba. A'a nayine domin kare mutuncina da martabata ta ɗiya mace. Sannan kuma hakan da nayi zai ƙara bani kariya daga hare-haren irinsu MD da basu iya ɓoye maitarsu a fili ga ƴaƴan mitane.        “Amarsu ta ango”. Daya faɗa ya sani ɗauke kai gefe ina murmushi. Shima ƙaramar dariya yayi yana dawowa ta inda na maida kan nawa. Ƙaramar harara na sakar masa ina sake ɗauke kaina. Ya ce, “Tab irin wannan harara haka amarya ai sai kisa na zube ƙasa wlhy. Kinga adana min ita sai nan da ƴan watanni kawai,  kinga inma suma nayi dai ƙya farfaɗo dani da kanki babu wanda yaji ko ya gani ko?”.     Dariya ya bani, amma kasancewar ba'a ganin bakin nawa sai nayi murmushi kawai na sake ɗauke kaina.            ★ Alƙawarin ALLAH ya cika. Iyayen Mansoor dai sun kawo kuɗi gidanmu a ranar juma'a. Ranar ni naga baƙin halin Mum muraran. Dan zage-zage ta dinga yi da yima Abba masifa wai an munafunceta. Ashe bai gaya mata ba sai ganin su kawu Musa yasa ta fara tambayarsa abinda ya kawosu. Shine ya sanar mata iyayen wanda yake nemana ne sukace zasu zo yau. Takaici ya sakata zuba masa ido kawai, amma ta kasa cewa komai. Dai-dai isowar baƙi kuma sai ga abinci Yaya Musaddiq na shigo da shi da ruwa da lemo batare da tasan daga ina aka dafo shi ba. Shiko Yaya Musaddiq sanin halinta da yay ne ya sashi saka matar ogansa ta dafa abincin. To ranar dai munga tujara. Dan nima da ban san mike faruwa ba ina a wajen aiki ina dawowa na samu rabona. Baby kuwa banda kuka babu abinda take yi. Ni dai ko uffan bance musu ba, a wajen Yaya Musaddiq kuma naji komai yanda ya kasance. Iyayen Mansoor sun kawo 300k, amma su Kawu Musa sun barma Abba 200k su sun ɗauki 100k na ɓangaren uba. Hakan da sukai baimun ba. Dan kamata yay su su ɗauki 50k Abba 50k aba Yaya Musaddiq 200k dan nasan dai shine mai mun wahalar ba kowa ba. Ban dai ce masa komai ba muka ci gaba da hira. Dan banama sha'awar shiga gidan. Ko hijjabi na ma da zan saka a gobe idan ALLAH ya kaimu domin zuwa taron can anan ɗakin Yaya na gogesa. Sai kusan sha ɗaya na shiga. Baby kawai na samu a falon zaune. Bance da ita komai ba na kama hanyar shigewa ɗakinmu.      Ji nai kawai an sakar min duka ta baya tare da damƙo hijjab ɗina. Da ƙyar naja numfashi saboda an shaƙe min wuya. Nai saurin riƙe hijjab ɗin ta gaba na yaga shi sannan na juyo ina sauke numfashi da ƙyar. Baby ce tsaye tana faman huci kamar mai shirin dambe. Na mata kallon sama da ƙasa kafin cikin mamaki na ce, “Lafiya kuwa baiwar ALLAH zaki shaƙeni kamar wadda ta ci miki bashi? Are you okay?”.          “A haukace nake dan uwarki. Kuma kaɗan ma na miki, wataran idan na shaƙeki har sai kin daina numfashi zan ƙyaleki. Dan haka ina mai gargaɗinki in har kina son ranki ki fita a sabgar Mansoor wlhy. Ki kuma bar ganin ya kawo kuɗi da sunan na aurenki, wlhy sai dai in bana raye hakan zata kasance. Dan yanda ban samesa ba kema baki isa samunsa ba jaka kawai ƴan karoro a gidan mutane mai ƙwacewa yaran gida samari su mayya”.        Murmushi kawai na saki mai faɗi dan wlhy ni dariya ma ta bani da tausayi. Bance mata komai ba nai shigewata ɗaki na barta tana ɗuran zagi kamar ba dare ba. Zuwa can kuma naji kamar maganar Abba sama-sama ita kuma tana kuka. Baki kawai na taɓe na gyara kwanciya dan so nake nai barci sosai kodan abinda zan tunkara a gobe in ALLAH ya kai mu. Sai dai duk da haka kamar kullum sai da na tashi nai ƙiyamullaili dan ya riga ya zame min jiki tashin a kullum, sai dai idan banda lafiya, amma ko prioud nake saina farka....      *_DAMA ACE....._*             (Dama ace) kalmace mai harshen damo. Zaɓa mata gurbi a nawa labarin shine cigaba da nutsuwar saurarensa. Kamar kullum yau ma sai da nai duk ayyukan gidan kasancewar nasan yau ɗin Mum a cike take da haushina. Hatta shi Abban ban san a wane matsayi ya ɗauki auren nawa ba. Dan daya dawo da ga sallar asuba na gaishesa sama-sama ya amsa min ya shige ɗaki abinsa. Ga Baby a gefe da marasa kunyar ƙannenta su Bibaa da Nabil. Shiri na nayi kamar yanda na saba, dan baƙin dogon hijjabin jikina har jan ƙasa ma yake. Ban biye ta maganar MD ba, na kawo kuma face mask na saka kamar yanda na saba shima baƙi, na ɗaura sirrin farin eyeglasses ɗina da har ana iya ganin ƙwayar idona fes. Sai ƙamshi dake fita a jikina mai daɗin tsiya na humra da turare. Yaya shike sayamin turare da duk wani nau'in kayan kwalliya na mata. Hatta kayan ciki da suturu shine ke saya min. Hakan yasa banjin ƙyashin duk sanda salary na ya shigo account na tura masa su gaba ɗaya a account ɗinsa batare dana cire ko sisi ba a ciki. To idan na ajiye mizanyi da shi. Duk wani abinda nake buƙata baya gazawa wajen saya min. Idan abin yayi ya shigo zaka sameni a layin farko cikin masu sakashi. Da harda Baby yake saya, amma ta ce masa yama bar wahala bata so. Koda ta faɗa ɗin bai daina saya ba. Sai da yaga bata sakawa sannan ya daina. Hakan kuma baya hanashi bata kuɗi akan ta saya abinda take so. Wannan kam sukan amshe ita da uwarta kuma baza'a sayi abin kirki ba kuɗin zai gantale. Hatta da data sakara Yaya sakamin yake da credit, sai daga baya ne ma Mansoor ya amshesa wannan. Dan haka Yayanmu kallon uba nake masa ba yayaba wlhy, dan ya share mana kukan maraici tuni sai dai na kewar iyaye da bazai taɓa gushewa ba ga ƴaƴansu. Amma ta ɓangaren rayuwa komai Alhamdullah.        Kamar yanda Yaya Musaddiq yay alƙawari shine ya ɗaukan a mashin ɗinsa da yasha wanki sai ɗaukar ido yake. Office ya kaini inda su Mansoor ke jirana dan da motar office zamu fita. Ba sauran abokan aikina ba hatta da Mansoor ƙuri yay kawai yana kallona cikin nuna mamakin ganin hijjab dana zuba har yana sharar ƙasa. Amma sai yay murmushi tare da kashe min ido ɗaya alamar yaji daɗin hakan da nayi. Nima murmushin nayi kawai na ɗauke kaina ina mai gaishesu. Duk suka amsa min da kulawa. Sai Davido ne ke magana akan shigar tawa. Ban tanka masa ba na shige mota abina na zauna batare da na yarda na kalla inda MD yake ba ko sau ɗaya, dan gaisuwa ma kaina a gefe nai masa. Naci sa'a dama sun gama loda komai dama ni suke jira. Kulsoom ma na ciki ita. Kusa da ita na zauna muka gaisa, sai gasu suma sun shigo. Da farko Mansoor na kula kusa dani yaso zama. Amma ganin yanda na koma jikin window muka saka bags ɗinmu a tsakkiya yasa shi haƙura ya zauna kujerar gabanmu, sai lokacin na ɗan saci kallon MD, yay kicin-kicin da fuska sai mazurai yake. Ƙasa nai da kai ina kwasar dariya, ɗan son banza an shirya ganin banza. To bata samu ba ai, sai a tafi wata tashar.......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑬𝒍𝒆𝒗𝒆𝒏_ ........Tun kafin mu fice duk sun cika motar da hira, ni dai ban saka musu baki ba face ma bitar questions ɗin dake rubuce dan karna kwafsa. Dan a nawa shirin ina son masa tambayoyin ne batare da takarda ba. Duk da ma dai har cikin waya na kwashesu gudun samun matsala. Lokaci ɗaya naji motar ta ɗauki shiru, kamar zan basar sai kuma na gagara hakan, dole na ɗago domin ganin abinda ya sakasu nutsuwa haka. To nidai banga komai ba face uban cinkoso na ababen hawa da titin ya samu tamkar ba safiya ba kuma weekend. Da ƙyar drivern mu ya kutsa ya samu wajen parking ma. Haka muka firfito kowannemu na bin katafaran ginin da kallo. Dan sai yanzu na fahimci abinda ya saka su yin shiru ɗazun. Gini ne da akayisa da wani kalar zallar gilashi mai garai-garai ta gabansa. Ga wasu manya-manyan symbols da hoton motoci masu shegen ƙyau da mashina irin na masu kuɗin nan. Da manyan haruffan baƙi an rubuta *_MAASH_*.        Tako ina jami'an tsaro ne, hakan yasa komai ke tafiya a nutse duk da alamu ma sun nuna duk wanda ka gani a inda motarmu ta samu damar shigowa to ba ƙaramin mutum bane, ko kuma dai yana da izinin zuwa wajen. Dan zuƙa-zuƙan motocine na nunama tsara. Yaku bayi kuwa na daga can tunkushe a titi an hanasu shigowa (🤥😞😏). Dan ƙa'idar sai ka nuna invition ɗin nan zasu bar motar ka ta wuce. A ƙafa muka cigaba da takawa saman lafiyayyen titin da aka ɗauka tun daga babban titi har zuwa cikin companyn. A dai-dai katafaren gate ɗin ma dai sai da muka nuna invition ɗin. Sannan akai searching namu aka tabbatar da bama tare da komai sannan muka shige bisa rakkiyar wani jam'i. Da alama wajen zaman ma a tsare yake kenan. Bazaka tabbatar da Companyn mugun ƙato na gaske bane sai ka shigo ciki. Ashe ta gaban duk wasan yara ne da ado kawai. Duk girman harabar an gyarata da uban decorations mai matuƙar ƙyau da ɗaukar hankali. Hakama an tsara kujerun zama cike da birgewa. Da ga can gefe abincine aka jera irin dai na taron ƴan gayun nan, dan ga masu zungura-zunguran hulinan nan irin nasu o,e a kitchen sun jeru kamar ƴan cocin yarabawa (😂lol). Mune ƴan jarida na farko da suka fara isowa, hakan ya mun daɗi, dan koba komai mun samu sits ɗin gaba a inda aka tsara domin ƴan jarida. Tuni su devido sun dasa camaras namu kuwa a inda komai bazai wucemu ba. Zuwan namu kamar ya buɗe ƙofa ne, dan sai ga mutane da ƴan uwanmu ƴan media nata shigowa a nutse babu wata hayaniya ko kace nace. Tun shigowarmu kuma tuni mun fara nuna komai live kamar yanda contract ɗin yake. Dan haka kusan komai daya fara da tushe kai tsaye ana fara ganinsa ne daga gidan tvn mu. Ni dai har lokacin ina a zaune dan ba'azo kan aikina ba. Kafin cikar awa guda waje ya gama cika taf da manyan mutane. Muryar mc kawai ake ji yana sanar da isowar manyan baƙi, sai mu kuma ƴan jarida dake namu bayanin domin gidajen tvn mu kai tsaye. Goma dai-dai dake tabbatar da duk wanda ake buƙata a wajen ya iso hatta da gwamna da sarki ma aka sanar da isowar mai gayya mai aiki. Wato *_Awwab El-Mu'azz Maashi_*. Tsitt wajen ya sake ɗaukar shiru kasancewar dai-dai nan zuƙeƙiyar baƙar mota da irinsu shugaban ƙasa kawai nake gani a ciki ta shigo. Ta gefe da gefenta da gabanta da bayanta kuwa wasu irin murɗa-murɗan basumadayen garada ne da gani kasan ba bugun Kano bane sai dai Lagos ɗin dan bamu da masu irin wannan suffar gaskiya😞. Su duka riƙe suke da bindigu kai kace zasu iya hana mutuwa ɗaukar wanda ke'a cikin motar ne😏. Har tsakkiyar filin motar ta shigo, inda mutanen dake a cikin motar bayansu suka fito a lokaci guda su huɗu. Mace ɗaya maza biyu. Wanda ke mazaunin driver ne ya buɗe booth da hanzarinsa ya ɗakko carpet maroon mai shegen ƙyau an rubuta *_Maash_* a jikinsa da golden mai ɗaukar ido. Yayinda macen baturiyar ta iso da sauri sauran mazan biyu a gefe da gefenta. Daka ganta kaga cikakkiyar baturiya. Duk tsaye sukai a ƙofar motar kowa cikin nutsuwarsa da kamewar girmamawa abin zam mamaki. (Humm jama'a MANDA fa duniya ce😜). Kusan minti ɗaya cif muna zuba idon ganin abinda ke faruwa kafin wanda ke gefen damar matar nan ya kai hannu jikin handle ɗin ƙofar ya buɗe tamkar mai gudun tashin yaro a barci. Wasu sakanni goma aka sake kwashewa kafin wani almurin baƙin takalmin haIf cover shoe mai adon golden ya sauka saman maroon carpet ɗin a hankali. Sai da aka sake jan wasu sakannin kamar uku sannan ɗayar ƙafar ma ta sauka baƙin wandon suit ya bayyana. Sannu a hankali sauran gangar jikin ma ta fito. Kaf wajen har masu ji da mulkin da kuɗin babu wanda bai bi wanna halitta da kallo da ga ƙasa zuwa saman ƙyaƙyƙyawar fuskar mamallakin jikin ba. Tsaye yake gam akan tsahonsa na tsayayyen namiji da babu ko ranƙwafawa. Suit ɗin jikinsa da basai an zauna ɓata lokacin lissafin kuɗin da suka lashe ba sun masifar zauna masa da tabbatar da shi a matsayin jaruminsa mai gara kan naira ta yanda duk yaso bisa damar da ALLAH ya bashi. Komai na jikin nasa baƙine, sai ɗan adon takalminsa da ta kasance golden da neck tie.. ɗinsa shima golden mai azabar ƙyau. Kamilalliyar fuskasa ma'abociyar kamewa da tsare gida ko nace baƙin hali a tsuke, sai kwantaccen gashin kumatunsa siriri daya zagaye bakinsa zuwa haɓarsa tamkar an zana ba biro. Yau ɗin ma dai akwai ɗan kunne ɗaya manne a kunensa, hakama zanen tattoo ɗinsa mai fuskar lion na nan zaune daram. Saɓanin hoto yau gashinsa ne a ɗaure kamar yanda mata ke parking sai dai shi nashi acan ta ƙasa ya ɗauresa har yana ɗan sauka jikin rigarsa dan babu kitso yau. Wanda bai sani ba tuni yake sakashi a jerin larabawa. Babu mai ganin idanunsa kasancewar sakaye suke a cikin eyeglasses mai masifar ƙyau daya ƙara fidda taswurar halittar ƙyawun hancinsa daya zauna ɗaram kan fuskarsa. Kafin kace mi tuni ƙamshinsa ya baje wajen kai kace mu namu turaren baida tasiri ne ko Companyn da suka wallafo namu basu iya zaɓar ƙamshi ba. Kai jama'a akwaifa ƙyawawa a duniya. Idan kaga wani sai kaga kamar ka yanka kanka ka ɓoye wuƙar ƙawai. Bily karfa ki zata wannan bayanin da nake zayyano miki a kansa ya wani birgeni ne. Mtsowww ko kaɗan..        Gaba ɗaya yaran nasa sake kame kansu sukai cikin nuna tsantsar girmamawa a garesa. Karan farko na ɗan taɓe baki takaici kamar zai halakani. Shike nan a wannan rayuwar in har kana da dukiya ka zama saraki ko mai mulki?. Kai wani abun ma da ake maka ko kai mulkin ba lallai ya samu ba. Dibi dai wannan mutumin yanda yake wani busar isaka da shan ƙamshi fuska tamm kamar wanda aka aikama saƙon mutuwar tsoffinsa.        Cikin isa da bajinta, a slowly tamkar wanda ake ɗauka a faifan video yay wani kalar haɗe hannayensa duk biyu a waje guda ya ɗagasu sama alamar gaisuwa wa duk jama'ar wajen. Kusan kowa dake wajen sai da sukai yanda yay ɗin idan ka cire gwamna da sarki. Sai ko ni ƴar balaja'un ku da saida Khulsoom ta zunguran amma na fuske naƙiyi, sai ma laɓe mata baki da nai na sake maida idanuna dake cikin glasses kansa ƙurr kai kace nice camara ɗin ma. Har inda aka tanada domin zamansa a tsakkiyar sarki da gwamna yaran nasa sukai masa rakkiya. Sai da ya zauna sannan suka koma ta bayansa suma duk suka zauna.         Isowar tasa ta saka taron fara motsawa yanda ya kamata. An fara da gabatar da addu'oi kafin gwamna yay bayani mai birgewa a matsayin uban taro, dan ya nuna jin daɗinsa da farin cikinsa matuƙa game da wannan cigaba da aka kawo jiharsa, yana kuma fata da kira ga wannan shugaban kamfani akan idan har yaranmu sun cancanta yana roƙon ace sun zama mafi rinjaye da zasu samu aikinyi a ciki, yana kuma fatan ALLAH yasa kamfanin ya zamewa Kano dama arewacin ƙasar alkairi baki ɗaya.      Kowa yaji daɗin bayanin gwamna. Dan zaka tabbatar da hakanne a fuskokin jama'ar dake a wajen ma. Sai sarki shima dai a matsayin uban taron. Sosai jawabansu suka ƙayatar suka kuma birge shima ɗin dai. Dan yayi kiranye sosai ga masu arziƙinmu da su shigo su kafa cibiyoyin kasuwancin a arewa domin matasanmu su samu aikinyi, hakan da zasu dingayi zai rage mana raɗaɗin rayuwa da ake ciki a wannan ƙarni. Zai kuma ƙarama matasan himma da nisantasu da ga shaye-shaye ko ɗaukar makamin da bai dace dasu ba a matsayin neman abincinsu ko zaman banza a bakin tituna mara amfani. Idan kuma har masu arziƙi suka cigaba da janye jikinsu da dukiyoyinsu da ga arewa to lallai watarana sai an wayi gari kowa ya zama abinda ba'a so. Idan kuma hakan da ba'a fata ta kasance ba arewan kaɗai ba, hatta su ma kudancin da wasu maƙwaftan ƙasashe zata shafesu, suma kuma ta nakasasu kamar yanda muma muke a nakashe yanzu. Bayan waɗan nan bayanan wasu masu muhimmanci ma sun sake biyo bayansu kafin shi ma ya miƙe........✍️           _(🤭Ni dai nace faɗi gaskiya dai Samraah bama son kwana-kwana😜 idan Yaya Maash ya miki ne sai ai miki hanya🥱, dan kunsan bana ni gaskiya ƴar team Yaya Maash ce. Mu dama muna gidan kuɗi babu kwana-kwana🤣👌. Saura naji wani yace kwaɗayi🙄dan ɗan uwanmu ne Ya Maash ɗin na jini🤯, ai gwajin jini kuma a gani🤥😌)._                 _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒍𝒗𝒆_ .......(Kutumelacy). Na faɗa a zuciya lokacin da yay sallama da wata jarumar muryarsa cikin yanayin mazantaka da nuna kamewa tamkar wanda akama dole, dan hatta lips ɗin ma da ƙyar yake motsasu. Bayan an amsa ya cigaba da miƙa saƙon gaisuwa da sannu da zuwa nan ɗin ma dai a fiffisge alamar maganar ta zame masa dolene ko kuma gayune ko kuwa girman kai irin na masu hannu da maiƙon kaza oho masa. Ga wata hausarsa da ta gama gurɓacewa da harshen ƴan kudanci ko nace harsuna da yawa dan tamkar ba cikakken bahaushen da akace an haifa a gari irin Kano ba. A wata gaɓar ma hausar ƙwace masa take sai dai ya kwakuso turanci ko faransanci ya maka a wajen ya kuma fuske ya cigaba da jawabinsa. Kuga wani ɗigimi, da dai a turancin ya tsaya da yafi, to waye ya wani iya faransanci anan?. Koda yake ban sani ba tunda naga taron duk nasu ne na masu jiki duk chocolates. Haka dai ya haɗa jawabin mintuna uku da ƙyar yana faman mana haɗin gambizar yaruka uku a lokaci guda da kai hannu saman kai ya murza tabbacin dai maganar ta dole ce a garesa. Hummm duniya makaranta, yo ALLAH na tuba su mu kuma indai zance ne ai ko akkun farkon ƙarni ta sama mana lafiya, duk da dai nima sai naso nake nawa surutun. Amma dai na ƙara ilimi, tunda naga yayin ƴar jan ajin nan ake da fidda zance ɗaɗɗaya billa sake kame kaina zan dingayi tunda ban sani ba ko nan gaba nima na kuɗance. Yo Bily abin ai na ALLAH ne, bafa zaune nake kurum ba daga aikin jarida sai na gida. Ina ƴar sana'ar sai da hijjabai da takalma duk da jarin bai wuci na dubu ashirin ba. To nadai fi su o'e ai masu cika gida da munsharin barci ko.        Duk da fa jawabansa sun ƙayatar sun kuma tsaru tamkar daga takarda yake karantowa ni ƴar iyar taku sai da na taɓe baki. Yayinda wajen ya ɗauki tafi gaba ɗaya, a cikin ƴan jaridar mu harda masu yin fito. Hakama wasu gungun samari ƙyawawan da kallo ɗaya zaka musu kasan akwai ƴan canji dan kamar sun zaɓo kansu ne dan ƙyau da gayu, bana kuma raba ɗaya biyu abokansa ne sai salute nashi suke suma dai cike da isa da ƙasaitar. A haka taro ya cigaba da tafiya cikin nutsuwa, mudai ƴan jarida munata ɗaukar rahotanni babu mai damar cewa komai a yanzu sai nan gaba. Dan ya bada damar a masa tambayoyi a karo na biyu da zai fito, amma akan abinda ya shafi Companyn kawai. Nikam na taɓe baki, dan na shiryo nawa questions ɗinne akan komai kuma in sha ALLAHU sai na masa su duka, dan zan fara da manya-manyan cikine da dole sai ya magantu koda baya son hakan.         Ana tsaka da sauraren jawaban sauran manyan mutanen wajen fitsari yay mugun matsata. Sosai hankalina ya tashi, na shiga dana sanin shan shayin da nayi kafin na fito. Tun ina daurewa har dai na shiga mutsu-mutsun da Khulsoom ta lura dani.      “Samraah lafiya kuwa?”. Ta faɗa tana tsareni da idanu. Fuskata dake cikin facemask a marairaice na ce, “Ina fa lafiya Khulsoom. Wlhy wani mugun fitsarine ya matseni kamar zai zubo. Dan ALLAH ki tashi ki rakani kada ayi abin kunya a bainar nasi. Maimakon mai buɗe Company ya zama topic of the day ni na zama.” dariya ta nema saki, amma ganin yanda na ɗaure fuska ya sata daurewa ta ƙunshe abarta. Cikin raɗa ta ce, “Kima Mansoor magana ya raka ki, dan wlhy tsoron waɗan nan jami'an tsaron da aka baza nake yi”.      Wata hararar na sake watsa mata a karo na biyu, batare dana tanka mata ba na miƙe dan gab fitsarin yake da zubowa. Kasancewar wajen tsitt yake babu wani hayaniya kuma kowa a zaune yake a nutsensa sai tashina ya jawo hankalin mutane da yawa gareni. ALLAH ya soni komai nawa a rufe yake, idan ka cire tafukan hannuna da yatsunsu suka ƙawatu da jan lallale, na tabbata yau da ace ba hijjab na saka ba wannan idanun na jama'a sai ya sakani sakin fitsarin a wajen. Gudun karna taka doka ko yin abinda zai jawo min kunyata kai tsaye na nufi security dake kusa damu sosai. Gaishesa nayi cikin girmamawa bayan na sauke mask ɗina dan karma ya fassarani da abinda bashi nake nufi ba sannan nai masa bayani. Hakan da nai kuwa ya sakashi jin daɗi, dan har I'd card ɗina saida na nuna masa tunma kan ya buƙata. Wata mace a cikin jami'ansu ya yafito da hannu, ta iso wajen tana mai ƙamewa da salute nashi. Nuna mata ni yay yace ta rakani restroom. Da girmamawa ta amsa masa nan ma. Sannan muka wuce ta can bayan Companyn. Na zata anan bayin yake, amma sai naga ta shiga dani ta wata ƙofa alamar cikin dai Companyn zamu shiga amma ta baya. Dan ta gaba an gama zagayesa da zaren nan mai ribbon kuma ba'a kai ga yankawa ba. Lallai dukiya tayi aiki a wannan waje, duk da fa inda muka shiga bawani ciki-ciki bane ba. Amma tsayawa kwatanta miki Bily walla ɓata lokaci zamuyi. Har ciki muka shiga tare da ita, ta nunamin bayin farko, godiya nai mata munama juna murmushi. Ina shiga wayarta ta fara ƙara alamar shigowar kira, dole ta fita a wajen domin amsawa. Har kuma na gama abinda nake na fito babu ita. Mamaki ya kamani na shiga waige-waige. Ganin dai da gaske bata a wajen na nufi neman hanyar da muka shigo. Sai dai kuma na rikice dan hanyoyin da yawa ne ashe duk iri ɗaya. Canki in canka na shigayi a tsakani, ganin dai ba ganewar zanyi ba na shiga binsu ɗai-ɗai ina taɓawa. Sai dai me kowacce na taɓa sai na jita gam a kulle. Tun ina ɗaukar al'amarin wasa har hankalina ya fara tashi amma dai na dake ina ƙarama kaina ƙwarin gwiwa. Hope ɗina na gab da barina gaba ɗaya wata a cikin ƙofifin ta buɗe. Ji nai kamar na saki ihu dan daɗi, sai dai banyi hakan ba na saki ajiyar zuciya ina mai rumtse idanuna da buɗewa, cike da zumuɗi na sake kama handle ɗin ƙofar na murɗa, ina ƙoƙarin danna kai ciki naja wani wawan birki sakamakon abinda naci karo da shi mai ɗimauta zuciya da tunani.        Sosai jikina ke rawa idanuna a matuƙar ware kansu. Ganin hankalinsu bai kawo kaina ba na sake jawo ƙofar sosai ta yanda bazasu iya ganina ba. Video recording na latso a wayata na fara ɗaukarsu. A dai-dai lokacin ya zare wuƙar da ga jikin mutumin, wani irin gurnanin ƙarasa fitar rai yayi ya ida zamewa da ga jikin bangon da yake yay ƙasa. Mutumin daya buɗe masa mota ɗazun ne a gefensa, gaban mutumin da suka kashe ɗin ya kai duƙe yana mai saka yatsunsa biyu a saitin hancinsa, a wani irin yanayi ya furta, “Ya mutu Sir”.       Kansa ya ɗauke tamkar baiji miya faɗa ba. Hakan yasa wancan ɗin miƙewa batare daya sake cewa komai ba shima ya buɗe wani farin ƙyalle. Wuƙar ya saka masa a ciki tare da handkerchief ɗin daya riƙeta, sannan ya bar wajen cike da takun isa, bathroom dake cikin ɗakin ya nufa. Kusan minti ɗaya da wasu sakanni sai gashi ya fito yana goge hannu da ƙaramin farin towel alamun wankewa yayi. Sai da ya gama goge hannun yana ƙoƙarin ajiye towel ɗin yake faɗin, “Lukman ya shigo da kayan can, ya fita da gawan zuwa can anguwan”.      Kai yaron nasa ya jinjina masa cike da girmamawa. Ƙofa ya nufo, dan haka nai saurin tsayar da video ɗin na koma wani ɗan lungu na lafe. Wajen sauri face mask ɗina dake a hannuna ya faɗi ƙasa. Cikin takunsa da baya fidda sauti ya fito, cak ya tsaya tamkar wanda ake controlling da remote yana kallo mask ɗina dake yashe a ƙasa. Sosai na waro idanuna waje ƙirjina na wani irin mahaukacin bugawa da sauri-sauri. Lokacin da yake ranƙwafawa yana ƙoƙarin kai pen ɗinsa mai masifar ƙyau ya ɗauka facee mask ɗin dashi jinai kamar numfashina zai rabu da gangar jikina. Sake lafewa nai sosai tamkar ina shirin keta bangon na shige ciki. Yayi kusan sakan ashirin yana kallon mask ɗin, sai kuma ya zaro wani ƙyaƙyƙyawan handkerchief a aljihunsa ya warwaresa ciki ya saka. Da baya-baya ya koma yana ɗan waige-waige, ƙofar ɗakin daya fito ya ɗan buɗe kaɗan, sai kuma ya maida ya rufe ya sake juyowa. Kusan taku goma ya sake tsayawa cak. Da sauri na kai hannuna kan bakina na rufe kamar zan saki kuka dan tashin hankali. A hankali ya juyo da alama dai yana ji a jikinsa akwai mutum a wajen. Bakina na sake dumtsewa tare da hanci ina mai runtse idanuna da ƙarfin masifa. Nafi mintuna biyu a haka kafin na buɗe a hankali, wayam na gani alamar ya fice. Cikin sauri na zame nai ƙasa ina mai janye hannuna da sakin numfashi mai ƙarfin gaske. Inaga tunda nasan kaina nai hankali ban taɓa cin karo da matsanancin tashin hankali irin na yau ba. Kisan kai fa, na mutum ba wani ƙwaro ko dabba ba. Lallai mutum abin tsoro ne, taya zakai tunanin wannan mutumin zai iya aikata wannan ta'asar, jibesa kamar wani mutumin kirki. Koda yake wanda ke iya zana tattoo a jikinsa ga ɗan kunne ya kuma ɗaure gashi a kai kamar wani mace ko yay kitso komai ma ai zai iya aikatawa. Aiko bazan taɓa yin shiru ba, dolene nai gaggawar nunama duniya wanene shi, yanzu kuma ya kamata a cikin taron nan ba sai anjima ba. Zaram na miƙe kuwa ina tattaro wayata dake yashe a ƙasa da sauri........✍️         _“🤯🤯Na rasa abin faɗa Samraah.  Yaya kin tona asirin nasa kenan?”._ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒍𝒗𝒆_ .......(Kutumelacy). Na faɗa a zuciya lokacin da yay sallama da wata jarumar muryarsa cikin yanayin mazantaka da nuna kamewa tamkar wanda akama dole, dan hatta lips ɗin ma da ƙyar yake motsasu. Bayan an amsa ya cigaba da miƙa saƙon gaisuwa da sannu da zuwa nan ɗin ma dai a fiffisge alamar maganar ta zame masa dolene ko kuma gayune ko kuwa girman kai irin na masu hannu da maiƙon kaza oho masa. Ga wata hausarsa da ta gama gurɓacewa da harshen ƴan kudanci ko nace harsuna da yawa dan tamkar ba cikakken bahaushen da akace an haifa a gari irin Kano ba. A wata gaɓar ma hausar ƙwace masa take sai dai ya kwakuso turanci ko faransanci ya maka a wajen ya kuma fuske ya cigaba da jawabinsa. Kuga wani ɗigimi, da dai a turancin ya tsaya da yafi, to waye ya wani iya faransanci anan?. Koda yake ban sani ba tunda naga taron duk nasu ne na masu jiki duk chocolates. Haka dai ya haɗa jawabin mintuna uku da ƙyar yana faman mana haɗin gambizar yaruka uku a lokaci guda da kai hannu saman kai ya murza tabbacin dai maganar ta dole ce a garesa. Hummm duniya makaranta, yo ALLAH na tuba su mu kuma indai zance ne ai ko akkun farkon ƙarni ta sama mana lafiya, duk da dai nima sai naso nake nawa surutun. Amma dai na ƙara ilimi, tunda naga yayin ƴar jan ajin nan ake da fidda zance ɗaɗɗaya billa sake kame kaina zan dingayi tunda ban sani ba ko nan gaba nima na kuɗance. Yo Bily abin ai na ALLAH ne, bafa zaune nake kurum ba daga aikin jarida sai na gida. Ina ƴar sana'ar sai da hijjabai da takalma duk da jarin bai wuci na dubu ashirin ba. To nadai fi su o'e ai masu cika gida da munsharin barci ko.        Duk da fa jawabansa sun ƙayatar sun kuma tsaru tamkar daga takarda yake karantowa ni ƴar iyar taku sai da na taɓe baki. Yayinda wajen ya ɗauki tafi gaba ɗaya, a cikin ƴan jaridar mu harda masu yin fito. Hakama wasu gungun samari ƙyawawan da kallo ɗaya zaka musu kasan akwai ƴan canji dan kamar sun zaɓo kansu ne dan ƙyau da gayu, bana kuma raba ɗaya biyu abokansa ne sai salute nashi suke suma dai cike da isa da ƙasaitar. A haka taro ya cigaba da tafiya cikin nutsuwa, mudai ƴan jarida munata ɗaukar rahotanni babu mai damar cewa komai a yanzu sai nan gaba. Dan ya bada damar a masa tambayoyi a karo na biyu da zai fito, amma akan abinda ya shafi Companyn kawai. Nikam na taɓe baki, dan na shiryo nawa questions ɗinne akan komai kuma in sha ALLAHU sai na masa su duka, dan zan fara da manya-manyan cikine da dole sai ya magantu koda baya son hakan.         Ana tsaka da sauraren jawaban sauran manyan mutanen wajen fitsari yay mugun matsata. Sosai hankalina ya tashi, na shiga dana sanin shan shayin da nayi kafin na fito. Tun ina daurewa har dai na shiga mutsu-mutsun da Khulsoom ta lura dani.      “Samraah lafiya kuwa?”. Ta faɗa tana tsareni da idanu. Fuskata dake cikin facemask a marairaice na ce, “Ina fa lafiya Khulsoom. Wlhy wani mugun fitsarine ya matseni kamar zai zubo. Dan ALLAH ki tashi ki rakani kada ayi abin kunya a bainar nasi. Maimakon mai buɗe Company ya zama topic of the day ni na zama.” dariya ta nema saki, amma ganin yanda na ɗaure fuska ya sata daurewa ta ƙunshe abarta. Cikin raɗa ta ce, “Kima Mansoor magana ya raka ki, dan wlhy tsoron waɗan nan jami'an tsaron da aka baza nake yi”.      Wata hararar na sake watsa mata a karo na biyu, batare dana tanka mata ba na miƙe dan gab fitsarin yake da zubowa. Kasancewar wajen tsitt yake babu wani hayaniya kuma kowa a zaune yake a nutsensa sai tashina ya jawo hankalin mutane da yawa gareni. ALLAH ya soni komai nawa a rufe yake, idan ka cire tafukan hannuna da yatsunsu suka ƙawatu da jan lallale, na tabbata yau da ace ba hijjab na saka ba wannan idanun na jama'a sai ya sakani sakin fitsarin a wajen. Gudun karna taka doka ko yin abinda zai jawo min kunyata kai tsaye na nufi security dake kusa damu sosai. Gaishesa nayi cikin girmamawa bayan na sauke mask ɗina dan karma ya fassarani da abinda bashi nake nufi ba sannan nai masa bayani. Hakan da nai kuwa ya sakashi jin daɗi, dan har I'd card ɗina saida na nuna masa tunma kan ya buƙata. Wata mace a cikin jami'ansu ya yafito da hannu, ta iso wajen tana mai ƙamewa da salute nashi. Nuna mata ni yay yace ta rakani restroom. Da girmamawa ta amsa masa nan ma. Sannan muka wuce ta can bayan Companyn. Na zata anan bayin yake, amma sai naga ta shiga dani ta wata ƙofa alamar cikin dai Companyn zamu shiga amma ta baya. Dan ta gaba an gama zagayesa da zaren nan mai ribbon kuma ba'a kai ga yankawa ba. Lallai dukiya tayi aiki a wannan waje, duk da fa inda muka shiga bawani ciki-ciki bane ba. Amma tsayawa kwatanta miki Bily walla ɓata lokaci zamuyi. Har ciki muka shiga tare da ita, ta nunamin bayin farko, godiya nai mata munama juna murmushi. Ina shiga wayarta ta fara ƙara alamar shigowar kira, dole ta fita a wajen domin amsawa. Har kuma na gama abinda nake na fito babu ita. Mamaki ya kamani na shiga waige-waige. Ganin dai da gaske bata a wajen na nufi neman hanyar da muka shigo. Sai dai kuma na rikice dan hanyoyin da yawa ne ashe duk iri ɗaya. Canki in canka na shigayi a tsakani, ganin dai ba ganewar zanyi ba na shiga binsu ɗai-ɗai ina taɓawa. Sai dai me kowacce na taɓa sai na jita gam a kulle. Tun ina ɗaukar al'amarin wasa har hankalina ya fara tashi amma dai na dake ina ƙarama kaina ƙwarin gwiwa. Hope ɗina na gab da barina gaba ɗaya wata a cikin ƙofifin ta buɗe. Ji nai kamar na saki ihu dan daɗi, sai dai banyi hakan ba na saki ajiyar zuciya ina mai rumtse idanuna da buɗewa, cike da zumuɗi na sake kama handle ɗin ƙofar na murɗa, ina ƙoƙarin danna kai ciki naja wani wawan birki sakamakon abinda naci karo da shi mai ɗimauta zuciya da tunani.        Sosai jikina ke rawa idanuna a matuƙar ware kansu. Ganin hankalinsu bai kawo kaina ba na sake jawo ƙofar sosai ta yanda bazasu iya ganina ba. Video recording na latso a wayata na fara ɗaukarsu. A dai-dai lokacin ya zare wuƙar da ga jikin mutumin, wani irin gurnanin ƙarasa fitar rai yayi ya ida zamewa da ga jikin bangon da yake yay ƙasa. Mutumin daya buɗe masa mota ɗazun ne a gefensa, gaban mutumin da suka kashe ɗin ya kai duƙe yana mai saka yatsunsa biyu a saitin hancinsa, a wani irin yanayi ya furta, “Ya mutu Sir”.       Kansa ya ɗauke tamkar baiji miya faɗa ba. Hakan yasa wancan ɗin miƙewa batare daya sake cewa komai ba shima ya buɗe wani farin ƙyalle. Wuƙar ya saka masa a ciki tare da handkerchief ɗin daya riƙeta, sannan ya bar wajen cike da takun isa, bathroom dake cikin ɗakin ya nufa. Kusan minti ɗaya da wasu sakanni sai gashi ya fito yana goge hannu da ƙaramin farin towel alamun wankewa yayi. Sai da ya gama goge hannun yana ƙoƙarin ajiye towel ɗin yake faɗin, “Lukman ya shigo da kayan can, ya fita da gawan zuwa can anguwan”.      Kai yaron nasa ya jinjina masa cike da girmamawa. Ƙofa ya nufo, dan haka nai saurin tsayar da video ɗin na koma wani ɗan lungu na lafe. Wajen sauri face mask ɗina dake a hannuna ya faɗi ƙasa. Cikin takunsa da baya fidda sauti ya fito, cak ya tsaya tamkar wanda ake controlling da remote yana kallo mask ɗina dake yashe a ƙasa. Sosai na waro idanuna waje ƙirjina na wani irin mahaukacin bugawa da sauri-sauri. Lokacin da yake ranƙwafawa yana ƙoƙarin kai pen ɗinsa mai masifar ƙyau ya ɗauka facee mask ɗin dashi jinai kamar numfashina zai rabu da gangar jikina. Sake lafewa nai sosai tamkar ina shirin keta bangon na shige ciki. Yayi kusan sakan ashirin yana kallon mask ɗin, sai kuma ya zaro wani ƙyaƙyƙyawan handkerchief a aljihunsa ya warwaresa ciki ya saka. Da baya-baya ya koma yana ɗan waige-waige, ƙofar ɗakin daya fito ya ɗan buɗe kaɗan, sai kuma ya maida ya rufe ya sake juyowa. Kusan taku goma ya sake tsayawa cak. Da sauri na kai hannuna kan bakina na rufe kamar zan saki kuka dan tashin hankali. A hankali ya juyo da alama dai yana ji a jikinsa akwai mutum a wajen. Bakina na sake dumtsewa tare da hanci ina mai runtse idanuna da ƙarfin masifa. Nafi mintuna biyu a haka kafin na buɗe a hankali, wayam na gani alamar ya fice. Cikin sauri na zame nai ƙasa ina mai janye hannuna da sakin numfashi mai ƙarfin gaske. Inaga tunda nasan kaina nai hankali ban taɓa cin karo da matsanancin tashin hankali irin na yau ba. Kisan kai fa, na mutum ba wani ƙwaro ko dabba ba. Lallai mutum abin tsoro ne, taya zakai tunanin wannan mutumin zai iya aikata wannan ta'asar, jibesa kamar wani mutumin kirki. Koda yake wanda ke iya zana tattoo a jikinsa ga ɗan kunne ya kuma ɗaure gashi a kai kamar wani mace ko yay kitso komai ma ai zai iya aikatawa. Aiko bazan taɓa yin shiru ba, dolene nai gaggawar nunama duniya wanene shi, yanzu kuma ya kamata a cikin taron nan ba sai anjima ba. Zaram na miƙe kuwa ina tattaro wayata dake yashe a ƙasa da sauri........✍️         _“🤯🤯Na rasa abin faɗa Samraah.  Yaya kin tona asirin nasa kenan?”._ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒉𝒊𝒓𝒕𝒆𝒆𝒏_ ......Humm Bily nayi yunƙurin hakan kamar yadda na faɗa miki. Sai dai ina miƙewa aka buɗe wata ƙofa da sai yanzu hankalina ya kai na fahimci a itane muka shigo tare da jami'ar nan ɗazun. Wani ne ya shigo da kaya a hannu, da alama Lukman ɗin daya faɗa ne. Jikin bangon na koma na sake lafewa, har sai da ya shige. Maimakon na sake yunƙurin fita sai zuciyata ke bani shawarar tsayawa naga yanda zasu fita da gawar. Ga kiran Mansoor sai shigomin ya ke da alama jirana suke. Sauƙina ma wayar a silent take. A plane mood na sakata, na sake shiga video recording. Ko sakan goma ba'ai ba sai gasu sun fito da gawar kuwa, duk da an naɗeta cikin wani abu jini duk ya ɓata mayafin. Da ƙyar na iya tsaida karkarwar da jikina ke min. Suna ficewa nai saurin fitowa da hanzari nabi bayansu nima. Inayi ina waige-waige. Maƙalewa nai ta jikin ƙofa ina cigaba da ɗauka har suka sakata a cikin motar. Ina ganin sun kammala Lukman ɗin ya shiga motar ɗayan na shirin juyowa ciki na sake komawa wani lungun da gudu. Dan kar yaji sautin hakkina hijjab ɗina na kama na cusa a bakina har sai da ya koma ɗakin, babu jimawa sai gashi ya fito da mopper yana goge duk inda jinin ya ɓata. Ganin ya sake komawa ɗakin na fito da sanɗa, ta hanyar da muka shigo nabi na fita. Inda wani zai ƙuramin ido tuni zai gane a gigice nake, gashi babu mask ɗin a fuskata yanzun. Dawowata wajen taron dai-dai ana mimmiƙewa zuwa inda ribbon ɗin nan yake. Hakan ta bani damar isa inda su Khulsoom suke. Bag ɗina kawai na amsa a hannunta na jefa wayata na ciro wani face mask ɗin na shiga sawa. Ganin yanda suka tsareni da ido ya sakani ɗaga musu hannu cikin dakewa na ce, “Kuyi haƙuri ina a inda bai kamata na ɗaga waya bane ba. Badai har yay jawabi na biyun ba ne ko?”.         Khulsoom ce ta amsa min da “A'a bai yiba sai an gama yanka abin can.” kai na jinjina mata alamar fahimta. Yayinda nake ɗan satar kallon Mansoor ta gefen ido, dan shi baice dani komai ba face zubamin idanu da yay kawai. Da alama bai gamsu da amsar dana bada ba. Dama nasan in kowa bai fahimci halin da nake a ciki ba shi sai ya fahimta. Dan akwai shaƙuwa ta musamman tsakanina da shi ta yanda ko motsi ɗaya daga cikinmu yayi sai ɗan uwansa ya fahimci mi yake nufi. Ban sake yarda na kalla inda yake ba muka nufi inda za'a yanka ribbon ɗin. Duk yanda naso kame kaina daga kallon mutumin nan na gagara haka. Mamaki abinda ya faru a cikin ƴan mintunan da basu wuce talatin ba kawai nake. Ban fahimci na tafi tunani mai zurfin da har bana fahimtar mi ake a gurin ba sai da Khulsoom ta zungureni. Numfashi mai nauyi na kawo tare da yin firgigit na ce mata, “Na'am mi kike ce?”.        Da mamaki ta ce, “mike damunki ne wai haka Samraah. Duk kinyi wani iri kamar wadda ke a rikice. Kalla yanda kike zufa ga hankalinki sam baya kan abinda ma akeyi”.     Cikin son basar da ita na ce, “Cikina ne ke ɗan juyamin. Inaga awaran da naci ne da kabeji ɗazun da safe.”          “Ayya sannu, amma tunda kin san yana baki matsala haka ai da baki ci ba, ke da zaki shigo cikin taro babu daɗi kaita zaryar toilet ai”.       “Haka ne, nima na shafa'a ne kawai. Amma in sha ALLAHU ina fatan ma bazan sake zuwa toilet ɗin ba. Akwai maganin da nake sha a bag ɗina bari na sha shi”.     Kanta ta jinjina min tana sake min sannu. Inda muke zaune na koma na zauna dan hakan sai yafi min sauƙi. A dai-dai nan aka saki tafi alamar har an yanka. Na sake tafiya a tunani naji saukar muryar Mansoor a kaina. Firgigit na dawo hayyacina ina kallonsa. Sai kuma nai saurin ɗauke idanun a kansa ina ƙoƙarin dai-daita nutsuwata.        “Samraah mike damunki?”.    In har kaji sunana kai tsaye a bakin Mansoor babu wasa sam a ciki. Saurin girgiza masa kai nayi da faɗin, “Babu komai fa. Na dawo nan nasha magani ne kawai”.      “Ƙarya kike”.   Ya faɗa kansa tsaye kawai. Nasan za'ayi hakan. Dan Mansoor ya gama sanina matuƙa kasancewarsa mutum mafi shaƙuwa a rayuwata bayan ƴan gidanmu. Shekara biyar ai ba wasa ba. Ƙasa nai da kaina kawai ina wasa da yatsun hannuna. Sai kuma na ɗauki wayata nai rubutu na tura masa. Ganin yanda ya cigaba da tsaiwa yana kallona ya sani ɗagowa ina masa nuni daya duba wayarsa. Baiyi musu ba ya zarota ya duba. Da sauri ya ɗago yana kallona. Sai kuma babu shiri shima ya kai zaune a kujerar kusa da ni. Sai da ya wawwaiga gefe da gefenmu sannan ƙasa-ƙasa ya ce, “Da gaske Baby”.        Kaina na jinjina masa kawai ina ƙoƙarin riƙe hawayen da suka ciko min ido. Sai kuma na kallesa na ce, “Ina son nabar wajen nan yanzu. Dan na yarda face mask ɗina a ciki ya ɗauka. Na tabbatar zuciyarsu dole tana musu wasi-wasi akan dole wani ya shiga wajen. Dan na fahimci hankalin yaron nasa kamar tun ɗazun ma ya rabu biyu akan mutane.”           “Ba tafiya bace mafita Samraah. Ki ƙara daurewa a kammala komai kawai. Sannan ki dawo da hankalinki jikinki, dan fitarki yanzu a wajen nan bazata zama mai sauƙi ba, sannan zasu ma iya ganewa ta hakan tunda baki da wani dalilin fita na zahiri. Kinga ma tashi mu shiga ciki kinga mutane sun kusa gama shiga za'a zagaya cikin companyn ne”.       Badan naso ba dole na miƙe. A zuciyata kam sai addu'oi nakeyi. Kar kiga fa kamar na cika tsoro. Wlhy babu abinda ke tada min hankali sai ganin gawar mutum cikin jini. Dan abune da bai taɓa faruwa da ni ba. Kinga ko sanda Babanmu ya rasu banda wani cikakken hankalin daya kamata irin hakan yaban tsoro. Tunda shima har aka binne gawarsa yana a yanayin zubar jini saboda accident. Mamanmu kuma bamma san rasuwarta ba sam, tunda ban wuci 3years ba kwata-kwata. Haka dai da ƙyar na cigaba da riƙe kaina mukabi ayarin ƴan ganin cikin companyn. Ya haɗu matuƙa gaya. Ga wasu manyan machines a wani ƙaton hall da baida iyaka. Da alama daga nan za'a dinga ƙera motocin ko haɗa su ne ma oho musu. Bayan nan akwai wajaje daban-daban masu ɗauke da abubuwa kala-kala da bamusan na miye ba, duk da wani bature a cikin abokan nasa sunata ƙoƙarin yin bayani, ni dai ba wani fahimtarsu nake ba sam. Dan duk yanda wajen ya kai ga haɗuwa a yanzu ni sam baya birgeni. Sai ma ganinsa nake baƙiƙƙirin da duhu. An ɗauki kusan mintuna talatin a ciki kafin a fito. Ɗayan sashen da ya kasance shine ake fara gani daga titi, wanda an yisane da zallar gilashi aka sake nufa. Anan ne offices ɗin ma'aikatan yake ashe. Tun daga hawan farko har zuwa na biyar sai da muka shishshiga da taimakon lift... Duka offices ɗin sun haɗu, hatta na ƙananun ma'aikata dake a hawan farko ma duk da na haɗaka ne komai tsaf. Amma nasa na matsayin oga kwata-kwata yafi kowanne tsaruwa, dan tamkar ba'a Nigeria kake ba. Daga office ɗin kuma akan iya ganin cikin ƙwaryar Kano da ƙyau ta kowanne ɓangare. Sosai abin akwai ƙayatarwa. Sai dai ni bai ƙayatar dani ba. Dan yanzu baƙiƙƙirin ma nake kallon mai Companyn kamar baƙin maciji. Nan ma an kwashi wasu mintuna kafin a fito. ALLAH ALLAH nake kawai yayi jawabin ƙarshen nan na masa tambayar da zan masa na bar wajen. Amma sai akace abinci za'aci a yanzun, sannan aje salla a dawo a ƙarasa. Kamar zan fasa ihu haka naji, sai dai yaya zanyi. Dole yanda suka tsara haka kowa zai bi. An fara gabatar da abincin a nutse, za kuma azo har inda kake a baka zaɓin abinda kake son ci sannan aje a kawo maka. Koda aka yambayen nikam nace a'a. Dan na ɗau alwashin bazanci kuɗin jinin mutane ba. Wama ya sani ko tsafi yake yi ne. Ai dama al'amarin dukiyar tasa da mamaki, shiyyasama mutane suketa wasi-wasi a kansa. Haba mutumin nan ai yayi ƙarami da tara irin wannan dukiyar haka. Kwata-kwata fa bazai wuce talatin ba. Inma zai haura hakan kaɗanne kuwa. Yo ko iya wannan companyn akace ya mallaka a shekarun nan nasa ai abin ayi wasi-wasi ne balle kuma ace yana da ninkin baninkin hakan har dasu jirage. Jirgi ake magana fa dake tashi sama da ɗaruruwan mutane bawai kwale-kwale na katako da ake tsallaka ruwan ɓagwai ba. Sannan bama ɗaya ba, ba biyu ba fa....          “Baby!!”.     Mansoor ya sake katse min tunani, dan yanzu a gefena yake. Firgigit na dawo hankalina. “please be smart mana. Ko so kike abokan tafiyarmu su fahimci wani abu ne?.”      Kaina na girgiza masa. Cikin dauriya na kalla abincin da ya saka a kawo min. Maimakon naji sha'awar cinsa kodan ƙyawun da yay a cikin ido ga kaza har rabi a ciki sai naji sam baya wani birgeni. A hankali na sauke a jiyar zuciya da ce masa, “Na ƙoshi da abincin nan wlhy. Kayi haƙuri dan ALLAH.”        Kallona kawai ya tsaya yi, ni kuma na ɗauke idanuna daga sashensa gaba ɗaya. Da ga ƙarshe ma na ɗauka wayata na shiga buga game wai duk dan dai na dawo da hankalina jikina. Sai dai tuni na kasa cigaba da buga game ɗin, na koma kallon mutane a ƙasan ido musamman ma yaronsa da duk wani motsin sa......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑭𝒐𝒖𝒓𝒕𝒆𝒆𝒏_ ........Kusan kowa da ke a wajen abincin yake ci. Amma banda sarki banda gwamna. A kansa idanuna suka sauka shima. Zaune yake ƙafa ɗaya kan ɗaya da takardu a saman cinyarsa yana dubawa. Gefensa baturiyar matar nan ce ke masa magana da nuna masa abinda ke a takardun. Babu komai a gabansa sai bottle ɗin ruwa alamar ba abincin zai ci ba shima. (Jibesa kamar na ƙwarai). Na ayyana a zuciyata cike da taicinsa, ji nake kamar naje na shaƙe mar wuya na kwarara ihu tare shelantama mutane wanene shi. Amma dai na dake. Mansoor ne ya farga da mugun kallon da nake masa, sunana ya kira a hankali. Hakan ya sakani dawowa hayyacina. Ina ɗauke idona daga inda yake kuwa yana ɗagowa shima. Da alama yaji a jikinsa ana kallonsa ne. Harararsa na ɗan yi ta gefen ido na ɗauke kaina gaba ɗaya da ga sashinsa.         Bayan duk an kammala cin abincin aka fara shirin shiga salla. Akwai ƙaton massalaci a cikin companyn. Ƙasa na maza, upstairs na mata. Sarki ne da kansa yaja sallar. Bayan an idar aka fito domin cigaba da abinda ya tara mutane dan lokacin tashi ya kusa. Zaune nai a massalacin na kasa fita. Sai da Khulsoom tai kirana a waya. Mansoor na samu a ƙofar massalacin tsaye yay shiru alamar yayi zurfi a tunani. Tsayawa nai kawai ina kallonsa, kafin na ƙarasa gabansa naɗan jujjuya hannuna a saitin fuskarsa sannan ya kawo numfashi. Alamar (lafiya?) Na masa da kaina. Ya sake sauke numfashi da sakin murmushi. “Lafiya Lau Babie. Damuwarki ce ta daman. Gaba ɗaya bana jin daɗin yanayin nan da nake ganinki a ciki. Dan ALLAH ki saki jikinki har mubar wajen nan zamu san mafita, kinga lokacin da zakiyi aikin ki ya kusa cika”.       Kaina na jinjina masa da faɗin, “In sha ALLAH zanyi ƙoƙarin hakan.”     Cikin gamsuwa ya nunamin hanya alamar muje. Babu musu muka jera har wajen zaman mu. “Cikin ne har yanzu dai?”. Khulsoom ta faɗa dai-dai ina kaiwa zaune. Guntun murmushi na mata ina girgiza kaina. “A'a na tsaya ƙarasa addu'a ne kawai. Ga zaman nan na waje ɗaya baka ɗan motsawa kuma akwai gundira”.       “Sosai ma kuwa. Bakiji yanda ƙafafuna sukai dayi ba. Amma ai an kusa tashi in sha ALLAH tunda naga ga shi ma yana shirin miƙewa yay jawabin ƙarshe. Sai ki shirya lokacin aikinki yayi”.     Jinai ƙirjina yay wani kalar harbawa. Har sai da na ambaci hazbinallahu wa-ni'imar wakil sannan na ɗan ji sassauci. Cigaba da ambaton hazbinallah... ɗin nayi, yayinda shi kuma ya fara jawabinsa. Kamar dai ɗazun haka yake faman gwamutsa mana gurɓatacciyar hausarsa da turanci da faransanci. Dan in yay hausar yaji ya kakare sai kawai ya kwakuso turanci ya maka abinsa..    Gaba ɗayanmu ƴan Jaridar da aka bari muka shigo wajen munzo da ga gidaje bai fi takwas ba ne. Dan haka tambayoyin da zamu masan ma daga inda muke zaune ne zamuyi su. Kuma za'ayi ɗaya bayan ɗaya ne. Bayan ya kammala jawabansa ya kawo dubansa garemu. Da yanayin gajiyawa dan hatta muryarsa ta nuna hakan ya furta, “Bismillah zaku iya yin tambayoyinku. Sai dai Please akan abinda ya shafi companyn nan kawai. Bana son wasu silly questions da basu shafi abinda ya taramu anan ɗin ba”.     Cikin gamsuwa duk suka jinjina masa kai, dan ni dai bakina na taɓe ina mai jan tsuki ciki-ciki da ni kaɗai naji kayana, wannan ma ai rainin hankali ne, yanama mutane magana a gadarance. Wani dattijo ne ya fara miƙewa rigarsa da tambarinsu ya fara tambaya. Idanu ya zuba masa tamkar bazaice komai ba, harma kowa yay tunanin ko bazai amsa bane sai akaga ya ɗan murmusa kaɗan iya lips ɗinsa dake ƴan ficit. Gasu pink sosai dan sun ciza. Sai kuma ya nuna PA ɗinsa dake bayansa alamar shine zai amsa wannan tambayar. Hakan kuwa akai PA ɗin nasa ne ya bada amsar, hakama tambaya ta biyu da ga wasu. Duk yanda naso na motsa nayi tamu tambayar na kasa hakan. Gashi mune kuma ya kamata ace mun ma zama na farko. Ganinfa bani da niyyar tashi kamar ma hankalina baya tare da su dan har ya rage saura ƴam gida ɗaya Khulsoom ta zungureni. Firgigit na dawo hayyacina. Sai dai kafin na tashi ma waɗan can sun tashi. Dole na haƙura har sai da ya amsa tasu sannan na ɗaga hannu da taimakon Khulsoom. Dama ya bani kamar yanda yake bama kowa.         A hankali na miƙe kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki. Yanda ya zuba min ido da ma kusan duk jama'ar dake wajen ya sani taune lips ɗina dake cikin face mask da ƙarfin tsiya ina mai karanto hazbinallah wa-ni'imar wakil a zuciyata. Da ƙyar na iya dai-daita numfashina ina mai janye idanuna da suma ke a cikin eyeglasses tare da sauke mask ɗin ƙasan haɓata sannan na furta. “Sir a matsayinka na matashi da za'a iya shiga mamakin ganin yanda ka gina katafaren kamfani irin wannan da ya zama na farko a Africa, a duniya na uku kuma bama shi kawai ka mallaka ba, akwai wasu manyan cibiyoyi daka kafa a ciki da wajen Africa ma ba Nigeria kawai ba, ko nace duniya, shin ko zaka iya jan hankali matasa irinka dake tasowa dangane da neman na kai da asalin tarihinka dan su san kaima ba daga kwance ka kai wannan matsayin ba, sai da kai aiki tuƙuru, tare da tsallake ƙalubale masu yawan gaske kuma duk kai haƙuri ka jure har gashi a yanzu ka zama wani babban ginshiƙi tauraron duniya dake haska yankinsa da ƙasarsa, yarensa harma da addininsa?”.            Bashi da naima tambayar ba, hatta sauran ƴan jarida ƴan uwana dama duk jama'ar dake wajen sai da suka zuba min ido, harma da masu hangame bakuna sama. Bama sai sun faɗi abinda ya basu mamaki ba, ni na sani. Yace kar a masa tambaya sai akan abinda ya shafi company, sannan tambaya ɗaya kacal zakayi. Amma ni dana tashi na haɗa kusan tambaya goma ne a cikin ɗaya, na kuma yi tambaya akan kamfani kawai da ya buƙata amma na saka abinda yake gudun a tambayesa ta yanda dolene sai ya amsa min ɗin. Yaja kusan mintuna biyu cif yana kallona kawai cikin wani irin yanayi, sai yatsun hannunsa daya dafe dogon tables ɗin da aka cika da mic.. yake ta motsawa, musamman biyun tsakkiya. PA ɗinsa ne ya ɗan yunƙuro amma sai ya ɗaga masa hannu alamar ya dakata. Tsayawar yayi, sai dai shima wani mugun kallo yake jefamin fiyema dana uban gidan nasa. Oho ko'a jikina, ni dai tunda nayi tambaya ta ai shikenan, amsa kawai nake buƙata. Motsawarsa da sakin wani shegen makirin murmushinsa ya saka kowa sake maida hankali kansa. Murmushin ya sake saki yana ɗan cizar lip ɗinsa na ƙasa. Yay wani ɗan diri-diri kamar wanda ya rasa abin faɗa sai kuma ya nuna ni yana sake sakin wani lalataccen murmushin. A hankali ya furta, “Hmmm you are very smart girl. A karo na farko na yarda zan bada wannan amsar, amma ba yau ba, ba kuma anan ba saboda munada ƙarancin lokacin hakan.”        Wani ƙwarin gwiwa ne naji ya sake zomin. Kai na tsaye na ce, “Thanks you sir. Amma taya zan sake samun wannan damar kamar haka ku da ganinku ba wasan yara bane. Gashi kuma ina matuƙar son gamsar da ƴan uwana matasa da sake farkar da waɗanda suka shagala. Zan so ace na samu date da time tun anan tare da location kodan ni da ƴan uwana matasa mu kasance a cikin shirin ji da ga bakin gwarzon mutum irinka”.          Ai da ƙarfi yanzu kam ya cije lips ɗinsa, yana wani kalar tsatstsareni da kaifafan idanunsa, dan duk da a cikin eyeglasses suke dolene ka fahimci hakan musamman yanda kai tsaye direction ɗinsa yake gareni. PA ɗinsa ne ya ɗan matso ya masa maganar da shi kaɗai ya ji abinsa. Yana gama faɗa masa ya ɗan ja baya kaɗan shi kuma ya juyo gareni. A bazata ga kowa ya furta, “Na baki dama, kisa date, kisa time ki faɗi location koda a office ɗin ku ne”.        Kutumelacy, ai jina ƙafafuna na neman gagara ɗaukata. Yayinda gaba ɗaya wajen yay wani irin ɗaukar shiru duk aka zuba masa idanun mamaki. Dan abune da bai taɓa faruwa ba. Maash a gidan tv ko jarida ko rediyo ko mujalla ana masa tambaya akan tarihinsa ba harkar business ba yana bada amsa. Abin mamaki. In taƙaice muku har taron nan ya tashi ban dawo dai-dai ba. Dan duk da hakan shine burina a kwanakin nan, sai nake jin kamar bazai yiwu ba. Koda yake hatta a ƙiyamullaili ɗina na satin nan sai da naita saka addu'ar fatan ALLAH ya ɗorani a kansa banyi zaton zan samu damar ba sam, kuma a cikin sauƙi ma haka. Hummm al'amarin da ban mamaki kam....             Kasancewar duk abinda ake a office ɗin mu suna kallo ne live dama mutane wata kalar gagarumar tarba muka samu. Musamman ma ni. Dan mata-matan staffs ɗin nan namu rungumeni suka dinga yi da kwarzanta ƙoƙarina. MD kam bakinsa tamkar zai yage ne. Wannan abin alfaharine a garesa ace mutum kamar Maash ya amsa gayyata da ga gidan tvn sa a gaɓar da kowa ke matuƙar buƙatar hakan. Oho su suke shirmensu ni nawa hankalin ma ba'a kansu yake ba. Maganar kisan can ne yay matuƙar tsaya mun a rai da zuciya. A dalilin sallar la'asar na samu damar zame musu. Dan bamu tsaya munyi acan ba kasancewar an tashi gab da za'a fara kiran salla. Ana idar da salla na MD yace muje gida mu huta. Haka dama nake buƙata. Dan burina kawai na keɓe da Mansoor na ji yaya za'ayi da batun video dake a cikin wayata. Muna barin office ɗin kam zancen dana fara masa kenan. Shima da alama abinda ke cimasa rai kenan. Dan haka muka shiga tattaunawa. Koda ya isa dani ƙofar gida ma ban fita a motar ba. Zancen muka cigaba da yi. Ni dai ina a matsayar mu kaima hukuma video ɗin. Tunda dai duk hanyar da zasu bibiyi batun gawar zai zama mai sauƙi kasancewar ya faɗi inda za'a kaita. Amma sai Mansoor ya ce nadai bashi dama yayi nazari tukunna. Na kuma tura masa video ɗin. Babu musu na tura masa, nima na adana wanda ke wayar tawa da ƙyau duk da babu wanda ke taɓamin waya ma. Daga haka mukai sallama ya wuce ni kuma na shiga gida. Dan Yaya Musaddiq na wajen aiki........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑭𝒊𝒇𝒕𝒆𝒆𝒏_ ........Daga ajiye Samraah gida ya wuce shima. Sama-sama ya amsa gaisuwar maigadin su ya shige ciki. Shi da ɗan uwansa a duk sanda suka dawo gida idan sun fita sukan fara shiga sashen iyayensu ne, musamman ma shi da akance yanada ƙulafucin uwa. Amma yau sai hakan ya gagara garesa. Dan ko motar tasa yau a gab da sashensu ya ajiyeta. A falo ya samu yayansa kwance cikin kujera yana kallo, hannu kawai ya ɗaga masa nan ma yay shigewarsa ɗakin barcinsa. Da kallon mamaki Attahir ya bisa. Dan abune da bai saba gani ba. Amma sai ya ɗan girgiza kai da sake maida kansa ga tvn da yake kallo, zuciyarsa na ayyana masa maybe ya gaji ne. Ya cigaba da kallonsa da tunanin idan yay wanka ai zai fito ya nema abinci, amma shiru kake ji har magrib na neman yi. Tsam ya miƙe ya nufin ɗakin nasa, ya ɗanyi knocking, kafin ma a amsa masa ya tura ya shiga. A tsaye ya samu Mansoor na faman kai kawo. Yay masa kallon tsaf sannan ya ce, “Kai wai lafiyarka ka kuwa? Ka dawo ma mutane kana ɗacin rai ka kuma shigo ka rufe kanka a ɗaki. Ko har ka fara tunanin auren ne? To bakai kace kana so ba, kama jirani kayi tsalle ka dire kai ba haka ba.....” Ganin Mansoor bai maida masa murtanin tsokanar ba yasa Attahir yin shiru, gabansa ya ƙarasa tare da dafa kafaɗarsa. Cike da kulawa ya ce, “Baka da lafiya ne Kiddo?”. Kai Mansoor ya girgiza masa. “To mike damunka?”. “Yaya babu komai fa. Kawai bana jin daɗine”. Jimm Attahir ɗin yay yana kallonsa. Sai kuma ya jinjina kansa da faɗin, “Okay shike nan. Shiga bayi kai alwala mu wuce massalaci. Dan kar Dad yay zaman jiranmu”. Kai kawai Mansoor ɗin ya jinjina masa yana nufar bayi. Attahir ya bisa da kallo har sai da ya shige. Shima kaɗa kansa yay ya fita yana ji a ransa ƙarya Mansoor ɗin ke masa. Duk da shi mutumin ne mara son hayaniya. Amma idan suna tare baka banbance wannan halin nasa na rashin yawan magana. Dan suna rayuwa ne tamkar abokai ba wa da ƙani ba. Sun tashi ne kamar ƴan biyu, komai nasu a tare yake. A halayyane kawai zaka iya banbance su. Dan tabbas sun banbanta tanan ɗin. Koda suka fito domin tafiya massalacin sun gamu da Dad ɗin su. Shima dai da mamaki yake kallon Mansoor ɗin. Harma ya gagara haƙuri ya ce, “Kai dama ka dawo gidan kabar Mamanku natama mutane shelarka?”. Kan Mansoor a rissine ya ce, “Dad amin afuwa na dawo ne kaina namun ciwo”. “Dole kai ciwon kai ai wannan hidima da kuka sha. Ku muje massalaci za'a tada salla”. Binsa sukai gwanin sha'awa suka fita har maigadi. Koda aka idar da sallar ma basu fito a massalacin ba har akai isha'i. A tare yanzu ma suka dawo gidan, kai tsaye ainahin sashen gidan suka nufa su duka. Sashene babba kuma mai ƙyau, dan komai yaji na ababen more rayuwa. Lallai gidan su Mansoor suna da kuɗi suma ba laifi. Dan idan wani ne ma zai iya cewa yafi ƙarfin aikin da yake yanzu, duk da kuwa yana a babbar kujera ne. Amma kuma aikin jarida hubby ɗinsa ne tun yana yaronsa. Sannan mahaifinsa nada babbar alaƙa ma da wajen aikin nasu, dan yanada hannun jari mai ƙarfi a cikin companyn. Shigowarsu dai-dai da fitowar ƴammata biyu masu kama da su Mansoor ɗin sosai daga wani ɗaki. Cike da murnarsu suka nufo Mansoor ɗin suna masa sannu, sai jera masa tambaya suke akan Maash. Amma a mamakin kowa ko a yaƙi ya furta, sai ma zagayesu yay ya wuce saman kujera ya zauna yana faɗin, “Malami kun isheni da surutu”. Babbar ce ta ɓata fuska tana kallon Dad ɗin su. Ya ɗan taɓe baki da ɗage kafaɗa alamar sunfi kusa. Sake ɓata fuska tai sosai. Ta ce, “Dad kallafa yanda yake basar da mu. Shi dama Yaya Man idan baiso abu ba ya iyama mutane wulakanci”. “To yayi fitinanniya.” Wata mata dattijuwa ta faɗa tana fitowa a hanyar dake tabbatar da kitchen ne, itama dai kama take sosai da su Mansoor ɗin. Hararar yarinyar tai da nuna musu hanyar data fito. “Ku wuce kuzo ku fiddo abinci. An gaya muku kowama irinku ne da shegen surutu. Yaro yaje aiki ya gaji kun wani sashi gaba dolene sai ya baku labarin abinda ya farun? Idan son gani kuke miya hanaku zuwa”. “To an taɓa ɗan lelen Mamy”. Cewar Attahir na ƴar dariya. Murmushi Dad shima yayi, yayinda Mansoor ya miƙe ya nufeta yana harar Yayan nasa. Yana zuwa gab da ita ya bata side hug, tare da kamo hannunta ya sumbata. A marairaice ya ce, “Mamy barsu kada ma kanki yay ciwo”. Kansa ta shafa fuskarta da murmushi. Kafin cikin kulawa ta ce, “Yaushe ka dawo?”. “Tun ɗazun ya dawo yau baya yayinki ne kawai Mamy”. Attahir ne ya faɗa yana kaiwa zaune a kujerar dining dan su Islam sun kammala jera abincin. Hararsa Mansoor yayi, tare da faɗin, “Mamy ƙyalesa so yake kawai ya haɗamu. Kaina fa ke ciwo amma nasha magani”. Yay saurin faɗar haka ne dan yasan yanzu zata iya ruɗewa. A hakanma tuni fuskarta ta nuna damuwa. Dan sai tattaɓa kan nasa take, daga ƙarshe dai ta ja hannunsa suka koma saman dining ɗin tana jera masa sannu, abincin ma a baki ta bashi dan kowa yasan ɗan gatan ta ne a gidan. Daurewa yay kawai ya ɗan ci abincin dan karta damu, amma gaba ɗaya hankalinsa na'a kan Samraah, babu abinda zuciyarsa ke hango masa sai yanda take a firgice har sanda ya ajiyeta a gida..... Bayan sun kammala cin abinci duk yanda Mamy taso suyi hira Mansoor bai cewa komai, zata nuna damuwa Dad ya dakatar da ita akan ta barsa yaje ya huta dole akwai gajiya. Mansoor yaji daɗin samun wannan damar, dan haka ya miƙe ya wuce sashensu. Yana shiga bedroom ɗinsa wayar Samraah yay ƙoƙarin kira. Cikin sa'a kuwa bugu uku ta ɗaga. Sai dai a yanda yaji muryarta na fita a shaƙe ya tabbatar har yanzu tana a cikin damuwa. Daɗaɗan kalamai ya shiga jera mata da lallashi akan ta kwantar da hankalinta. Ba shi yace mata zasuyi wani abu ba. Bafa itace ta aikata laifin nan ba da har zata takurama ranta haka suma dake tare da ita ta sakasu a damuwa. Sosai lallashin nasa yay mata tasiri, dan haka ya yanke kiran yana cewa bari yay shirin barci zai kirata video call. Yana yanke wayar Attahir na shigowa ɗakin, yanda ya kafesa da ido ya sashi duƙar da kansa, fatansa dai ALLAH yasa baiji wayar da sukai da Samraah ɗin ba. “Mike damunka Mansoor?”. “Yaya nace maka babu komai”. “Ƙarya kake yi. Idan kuma zakama kowa wannan ƙaryar ni kasan bazaka mun ba. Dan nasanka fiye da yunwar cikina. Koka sanar min, ko yanzun nan naje na kira maka Mamy da Dad maybe su ka sanar musu”. Ya ƙare maganar da juyawa kamar zai fita. Da sauri Mansoor ya riƙosa yana girgiza kansa. “Please basai ka kirasu ba. Ba wata damuwa bace mai yawa fa”. “Kasan dai bama ɓoyema juna damuwarmu. Karka fara daga yau to”. Numfashi mai nauyi Mansoor ya sauke tare da ajiyar zuciya. A ransa kuwa yana harhaɗo ƙaryar dazai sanar masa dan bazai taɓa faɗa masa gaskiyar zancen ba tunda yayima Samraah alƙawarin haka.....         ★💫★💫★💫★💫           “Sir dan ALLAH kada ka saka kanka a damuwa. In dai batun yarinyar nan ne dai-dai yake da kaɗawar iska mai wucewa. Ita ta isa ta saka abinda bakayi niyya ba. Waye ubanta a ƙasar nan? Har micece ita a aikin jaridar ma. Yarinya ce fa ƙarama fitik”.        Idanunsa dake lumshe ya buɗe a hankali. PA ɗin nasa dake magana ya zubama su kusan sakan arba'in. Sai kuma ya sake maidasu ya lumshe a kasalance. Dai-dai nan drivern sa yay sallama a ƙofar katafaren falon. PA ɗinsa ne ya amsa. Sai kuma ya bashi umarnin ya shigo dan yasan kayan boss ɗin nasu ne dake a mota ya kawo. Cike da tsantsar girmamawa yaje Centre table ɗin gabansa kuwa ya ajiye. Sai kuma yay ɗan jimm a duƙe kafin ya ɗago yana nuna wata jaka. “Sir wannan wani mutum ne yanzu nan ya kawo wai a baka. Naso ƙin yin hakan amma kausasan kalamansa suka daƙileni. Dan ya tabbatar min ƙin baka ɗin zai zama kuskuren da bazan yafema kaina ba kaima kuma bazaka yafe min ba. Dan saƙon nada amfanin da idan na wofamtar da shi dai-dai yake da gina harsashin tarwatsaka. Amin afuwa shine ya faɗi hakan”.        A zabire PA ɗinsa ya furta,  “What! Wane ɗan iska ne haka. Su securitys ɗin gate kuma suna aikin mi ya shigo cikin gidan nan, kai kuma ka zauna sauraren wawancinsa, are you mad?”.        Shiko gogan ko motsi baiyi ba. Sai idanunsa da ya ɗan buɗe kaɗan a ƙasa-ƙasa yake kallon drivern nashi da su. PA zai sake magana ya masa alamar ya barsa. Hakan yasa driver tashi da sauri ya fita ya bar saƙon da aka nannaɗe a cikin leda mai ƙyalli. Sake maida idanunsa yay ya lumshe kawai. PA da hankalinsa gaba ɗaya ke'a kan saƙon sam ya kasa nutsuwa, ganin ogan nasa baida alamar bashi umarnin ya buɗe suka miye a ciki ya furta, “Sir ya kamata musan minene a ciki. Dan bamu san mi mai saƙon ya taka ba har yake irin waɗan nan kalaman.” shiru kamar bazai ce komai ba, sai kuma ya kaɗa masa kai alamar ya buɗe ɗin. Jikin PA har rawa yake wajen ɗaukar saƙon. Kamar ƙyaftawar ido ya gama buɗesa ledar da aka nannaɗe sa. Sai dai kafin ya ciro abinda ke'a cikin kwalin da aka naɗe ɗin text message ya shigo wayarsa. Kasancewar wayar mai muhimmanci ce dan ta business ce ya ɗauka dan ya duba saboda akwai saƙon da dama suke tsammani. Rubutu ne da bai wuce words ɗari ba. Dan haka ya fara karantowa.            Sosai jikin Hayatu PA ke rawa yana mai ambaton “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Sir tabbas hasashenka ya zama gaskiya. A kwai wanda ya gammu, kuma tabbas shine mai face mask ɗin nan. Dan gashi anan ya turo saƙo?”. Idanunsa ya ɗan buɗe batare daya tanka ba yay masa alamar miya faru?. Cikin rawar jiki Hayatu ya fara karanto saƙon a fili kamar haka.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑺𝒊𝒙𝒕𝒆𝒆𝒏_ ........*_Barkan ka madubin wannan ƙarni. Ba sai na cikaka da gaisuwa ba, bari na tafi kai tsaye kawai. Ina buƙatar naira miliyan ɗari biyar daga gareka. Kuma cikin gaggawa. Idan ba hakaba, a daren yau zan rusa duk wani tanadinka da tunƙahonka da videon dake hannuna ta hanyar yaɗashi a social media. Kasan dai kisan kai ba abune mai sauƙi ba. Musamman ga mutum irinka sananne mai tarin magauta da masoya tako ina. Na baka awa arba'in da takwas. Idan kunne ya ji jiki ya tsira._*          Ya jima bai motsa da ga zaman da yay a lallausar kujerar ba ƙafa ɗaya kan ɗaya. Yayinda bayansa ke kwance jikin kujerar kansa a sama kaɗan. Yanda yay biris ɗin sai ka ɗauka baima ji ko fahimtar abinda PA ɗin nasa ya karanto masa bane ba sam. Yaja kusan minti uku PA nata kai kawo kafin yaja wani irin huci ya furzar yana mai buɗe idanunsa da suka sake wani irin garai-garai ai nahin suffarsu ta idanun mage na sake bayyana a fili. Zaune ya tashi da ƙyau, sai dai a nutsensa yake abin mamaki. Goran ruwa dake a Centre table ɗin ya ɗauka. Batare da yabi takan kofin dake kusa da ita ba ya ɓalle murfin kawai yakai bakinsa ya fara kwankwaɗa. Sai da ya shanyesa tas sannan ya jefar da bottle ɗin. Sake furzar da huci mai zafi yayi a karo na biyu yana sake nutsar da kansa, sai kuma kamar wanda ya tuna ya dubi PA ɗinsa. “Ina buƙatar duka cctv footage na company a daren nan?”.       Cak Hayatu ya tsaya da ga kai-kawon da yake, sai kuma jiki a sanyaye ya ce, “Sir ka manta mun duba sanda muka shiga kafin faruwar abun amma basayi duk an kashesu”.          “Hakane, amma kamar na kunna ukun farkon nan.”       “Yes yes tabbas kuma hakane fa Sir. Wlhy sai yanzu na tuna. Aiko ko wanene wannan zaici ubansa.” baima jira umarnin ogan nasa ba ya fice da sassarfa tamkar zai kifa ƙasa duk kuwa da dare ne a lokacin. Dan kusan sha ɗaya ma ake nema, saboda bayan an tashi a taron company sun bu sarkine kamar yanda ya buƙa. Bayan sallar magrib suka bar gidan sarki, maimakon gida suka wuce wajen wani abokin harƙallarsa dan haɗuwar ta sirrice, sai goma saura suka nufo gida. Gashi yanzu ana harar sha ɗaya da wasu mintuna.         Shima da ƙyar ya iya miƙewa da ga falon ya nufi bedroom ɗinsa. Tamkar mai hasashen ganin wani abu sai da ya gama kalle kowacce kusurwa da lungu da saƙon na ɗakin sannan ya kai zaune a bakin katafaren lafiyayyen gadon. Sabon gida ne fil dan yau ne ya fara shigarsa. Anyi aikin gininsa tare da Companyn nasa ne. Bai cika son zaman hotels ba a rayuwarsa sai in har ya zama tilas a garesa. Ta wani ɓangaren kuma gorin mutane akan kullum yana cika bakin shi ɗan Kano ne amma ko gida baida a arewa ma gaba ɗaya ya sashi ginin wannan gidan da ko makaho ya laluba yasan an kashe kuɗi. Dan yanda companyn ya haɗu shima gidan haka ya haɗu matuƙa.          Yanda ya zauna shiru ya dafe kansa zaka ɗauka ciwo yake masa ne. Amma sam ba haka bane. Abubuwane kawai suke masa kai-kawo a rai da suka faru a wannan yinin. Kallon komai yake tamkar wani film ba zahiri ba. Ba yau ne ya fara cin karo da matsaloli da ƙalubalen rayuwa ba. Amma na yau ɗin na musamman ne. Dan duk sunzo masa a bazata. Hakan na nufin ya sakankance da yawa kenan. Sannan dole ne ya sake shiri in har yana buƙatar abubuwa su tafi masa a yanda yake buƙata anan batare da tangarɗa ba?. Amma dai bari ya jira P.A ɗinsa da sakamakon da yake buƙatar gani kafin ya tsara komai akan mizaninsa. Da ga haka ya miƙe yana mai fara zame kayan jikinsa domin shiga wanka...         Yaja tsahon lokaci a bayin kafin ya fito sanye da bathrobe ash color sabuwa dal. Dan yanda take wani maski-maski zai tabbatar da hakan. Ƙaramin towel da a hannunsa ya kai kan jiƙaƙƙiyar sumar kansa mai tsaho data kwanto masa a fuska sosai, hakama ta bayansa kai kace bai haɗa jini da babaƙen fata ba balle ma har a kirashi da suna bahaushe. Tamkar ba shi kaɗaine a ɗakin ba. Fuskar nan a tsuke babu alamun rahama a cikinta. Duk da tun fitowarsa wayarsa ke tsuwwa alamar kira na shigowa, yay biris da ita tamkar bai ji ba. Sai ma ƙoƙarin nufar ƙaton mirrorn dake a ɗakin yayi abinsa. Tuni Hayatu ya shirya masa kayan shafe-shafensa a mirrorn, dan zaiyi kamar 1week ne a cikin Kanon kamar yanda yake fata. Hand dryer da aka ajiye a saman mirror ɗin sabuwa fil ya ɗauka ya jona a socket, sumar tasa ya fara busarwa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya kammala gyarata alamar ya riga ya saba da hakan. Kafin ya ɗan shafa mansa sama-sama tare da sprays masu shegen ƙamshi kala har biyu sannan ya nufi doguwar wadrobe data cinye bango guda. Ta farko kawai ya buɗe, anan ko yaga kaya kusan kala goma duk ƙananu, sai ƴar akwatin da yazo da ita da suit kala uku a ciki. Yasan kayan dake a shiryen duk aikin Hayatu ne. Batare da yace komai ba ya ciri farin pyjamas mai shegen ƙyau da laushi, sai boxer shima dai sabo. Tsaf yay shirinsa tare da sake komawa gaban mirrorn yay sabon wankan tsadaddun turarurrukansa na barci da ƙamshinsu ba'a magana kamar ba dare ba. Tsaki yaja a hankali yana hararar wayarsa da ke cigaba da tsuwwa babu ko ƙaƙƙautawa. Ya san mai kiran nasa, dan ita kaɗaice take karya dokarsa akan hakan. Duk wanda ya sanshi yasan yanada doka a akan kira, dokar kuwa itace in har kamasa kira 1 bai ɗaga ba ka bada mintuna kamar biyar sannan ka sake. Idan nan ma aka samu akasi bai ɗaga ɗin ba to ka haƙura kawai, idan shi ya samu lokaci zai iya ya kiraka, idan bai biyo ba kuma ka ɗauka kiran naka baida muhimmanci ne. Wayoyinsa duk a hannun Hayatu suke. Wannan ce kawai yake riƙewa saboda Ummien sa. Gaban gadon ya ƙarasa in da ya yasar da wayar, cikin ƙara ɗaure fuska ya ɗauka dan yana son ta barsa. A daƙile ya kai wayar kunensa sai dai yaƙi cewa komai. Sai da yaja kusan sakan hamsin ya ce, “Thanks”. Kawai yaja bakinsa yay shiru. Kasancewar bai sauke wayar ba zai tabbatar ma da har yanzu magana ake daga can, dan sai wani yamutsa fuska yake da sake tsuketa kamar mai jin warin mai maganar. Kusan minti biyu ya sake furta, “Zanyi barci”. Daga haka ya yanke kiran gaba ɗaya. Wayar ya wurga a saman gadon tare da jan tsaki mai ƙarfi ya haye gadon yay kwanciyarsa. Kai kace ma baida wata damuwa a rayuwa. Sai da yay addu'oi barci sannan ya lumshe idanunsa. Kafin wani dogon lokaci ya fara sauke numfashi a hankali alamar yayi barcin.....      ●´⌓`●●´⌓`●●´⌓`●            Duk yanda nagaji na kasa barci. Sai faman juye-juye nake abubuwa na dawo min tamkar yanzu suke faruwa, dan ma ƴar wayar da mukai da Mansoor ta ɗan sani ƴar nutsuwa. Ganin ƙwaƙwalwata na neman tarwatsewa na tashi na ɗaura alwala. Salla na farayi, sai da na kwashe kusan awa ɗaya da rabi sannan na zauna ina istigifari. Kamar a mafarki naji wayata na verbration. A gogo na kalla, ƙarfe biyu da kwata. Mamaki ya kamani, dan ko Mansoor baya kirana a wannan irin lokacin, kuma ma ai munyi waya duk da dai yace zai sake kira video call amma bai kira ba, ganin lokaci haja yasa ban damu ba. Dan duk tsawon wayarmu baya wuce daga tara zuwa goma. Jin an sake kira bayan ta katse na yunƙura na ɗauka. Abin mamaki Mansoor ne. Ɗagawa nai hankali a tashe, a tunanina ko wani abu ya samesa. Amma sai naji yaymin sallama cikin taushin murya. Ajiyar zuciya na sauke a hankali, sannan na amsa masa. “Dama naji a jikina zaki iya kasa barci, kiyi haƙuri Yaya ne ya ɗauke hankalina shiyyasa ban sake kiran ba. Haba Babie dan ALLAH ki cirema kanki damuwar nan. Ai ko ke kika aikata laifin nan sai haka”.      Numfashi na sauke a hankali. Cikin sanyin murya na ce, “Ni ban kasa barci ba fa, na farka ne kawai”.               “Uhhm yau kuma halin daba naki ba kika aro, to ai bai miki ƙyau ba dan baki iya ƙaryarba tunda ga harshenki yana rawa”.      Ɗan murmushin ƙarfin hali nayi, sai kuma nakai kwance ina faɗin, “To amin afuwa gashi na kwanta. Amma kaima miya hanaka barci?”.         “Saboda mahaɗin zuciyata batayi ba”.        “Humm”. Na faɗa kawai ina murmushi. Shima ina jiyo sautin nasa murmushin. Mun ɗan yi shiru na wasu sakannin kowannemu na sauraren saukar numfashin ɗan uwansa. Kafin ya katse shirun da cewa, “Kin sanarma Yaya Musaddiq abinda ya faru ko?”.       “A'a”.    “Miyasa?”. “Kawai dai”. “Aiko Babie ya kamata ya sani. Dan ko zamu iya ɓoyema kowa shi banda shi. Maybe ma ya ƙaremu da shawara ai. Dan wlhy har yanzu ni kaina duk a kulle yake”.        “Hakane zan sanar masa gobe in sha ALLAHU. Amma ni dai dan kaƙi ta nawane. Hukuma kawai ya kamata mu miƙawa ai”.      “Baƙi naiba Samraah. Ina son ki fahimci wani abu. Mutumin nan fa ya wuce duk inda kike tunani a ƙasar nan. Yanzu koda mun miƙa video ɗin nan ga hukuma kina ganin zasu hukuntashi ne. Ko kin manta yanzu a ƙasar nan tamu KUƊI ne ke magana ba GASKIYA ba. Shi kuma ALLAH ya bashi su, Samraah Maash fa zai iya juya Africa a tafin hannunsa ta yanda yaso bama Nigeria ba. Ke hatta da ƙasashen masu jajayen kunnuwan yanada ƙarfin faɗa aji sosai fiye da yanda kike tunani ta wasu fannoni. Sai dai su banbancinsu damu zasu iya hukunta duk wani mai laifi koda shi wanene? Amma a ƙasarmu ba haka bane. Ko wanda bai kama ƙafar Maash ba zai iya shallakewa in har da kuɗi. Kiyi haƙuri dai mu nema mafita mai ɓullewa. Mu kuma samu jajirtaccen ɗan sandan da zai iya yin duk abinda ya dace batare da kuɗi sun iya tankwarashi ba saboda gaskiyarsa. In dai Maash ne bazamu ƙyalesa ba sai an ƙwatoma mutumin nan hakkinsa”.         “ALLAH ya tabbatar to. Na kuma gamsu da bayaninka.”      “Masha ALLAH dear, yanzu dai zan shigo gobe in ALLAH ya kaimu ki biyo Yaya Musaddiq gareji mu haɗu acan dan ina so mu tattauna da gaggawa mu nemo mafita kafin Maash ya farga. Saboda babu yanda za'ai ace babu camaras a wajen nan duk da Companyn bai fara aiki ba sai Monday”.       Sosai zancensa ta ratsani dan har sai da na tashi zaune dingangan. Amma na gagara cemasa komai saboda yanda zuciyata ke bugawa da sauri-sauri........✍️        _Tofa masu karatu yanzunne fa ainahin wasan zai fara. Dan da alama mun gama sharar fage zamu tafi mataki na biyu a labarin. Wa kuke tunanin ya rubuta saƙon nan? Sannan karku manta a cctv footage fa Samraah za'a gani. Shin ko itace dai ta rubuta saƙon? Ko kuma wani yaji sanda take faɗama Mansoor yay amfani da damar? Ko kuwa ba ita kaɗaice ta gani ba? Shin minene dalilin Maash nayin kisan nan ma wai? Wanene aka kashe?..... Kai kai kai cakwakiya ce fa iya cakwakiya a labarin nan. Amma dai ina son jin amsoshinku a comment section. Yau har masu laɓe su fito inba haka ba gobe babu posting sai bayan salla🚴🚴🚴._ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑺𝒆𝒗𝒆𝒏𝒕𝒆𝒆𝒏_ .......*_WASHE GARI_* kamar yanda na saba na tashi nai ayyukana da sauri-sauri. Ana idar da sallar asuba nai wanka. Breakfast ɗin Yaya Musaddiq na ɗauka na nufi kai masa kusan bakwai da rabi. Nako samu har ya kammala shiryawa. Tunda na shigo yake bina da kallo, basai nace komai ba nasan ya gama fahimtar yanayina ne. Amma sai na dake. Sai dai ina gaishesa maimakon amsa min tambaya ya jeho min. Baki na buɗe zance babu komai yay saurin ɗaga min hannu da faɗin, “Karma kimun ƙarya. Faɗamin mike damunki?”.       A hankali hawayen da nake riƙewa suka silalo. Nima babu shiri na silale ƙasa ina mai fashewa da kuka. Duk abinda ke a raina tun jiya ne ya samu damar fitowa. Kafin ma ya sake cewa da ni komai na shiga faɗin, “Yaya kisan kai yayi. Da idona na gansa yana zare wuƙa a jikin mutumin ga jini face-face. A kunnena naji yana faɗin akai gawar wani anguwa a ajiyeta.....”           A cikin matuƙar tashin hankali ya katseni jikinsa na rawa. “Waye wai? Ki min magana a buɗe Samraah Please wa aka kashe waye kuma yay kisan?”.     Maimakon bashi amsa sai na miƙa masa wayata kawai. Amsa yay da rawar jiki. Yana ko dannawa da video ɗin ya fara cin karo dan ni bana sakama waya password sam. A matuƙar birkice ya ɗago yana kallona tun a fara kallon video ɗin. Idanunsa a warwaje na shiga razana ya furta, “Samraah Maash fa?”.       Kaina na jinjina masa da sauri ina faɗin, “Shi yaya! shi! Mutumin nan azzalumi ne bana kirki bane kamar yanda duniya ke kallonsa. Zata iya yiwuwa ma kuɗin nasa bana ALLAH bane na jinin mutane ne”.      Tuni zufa ta wanke Yaya Musaddiq. Cikin tashin hankali ya ce, “Bayan ni wa kika faɗamawa?”.           “Mansoor ne kawai Yaya. Tun jiya nace mu kai ma hukuma video ɗin amma ya hana. Shine ma yace na baka ka gani dan mu haɗu da shi a gareji mu tattauna”.      “Gara daya hanaki Samraah. Dan dole wannan al'amarin na buƙatar nazari. Maash ba anyhow mutum bane da dokar hukuma zatayi tasiri akansa cikin sauri. Inaga yanzu ba zama zamuyi ba tashi mu wuce. Bara na kira Mansoor ɗin ya fito shima gara muyi abinda ya dace da wuri tun kafin ya bar garin nan. Dan bai zama lallai a sake samun irin wannan damar ba duk da naji ya amsa miki wai kiyi hira da shi. Ga gari nan duk ya ɗauki zance harda masu faɗin ba haka kawai kikaje masa ba akwai asiri saboda yanda ya amsa ɗin babu musu a gaban duniya. Amma ni zuwa yanzu na fara zargin akwai wata a ƙasa kam, bana raba ɗayan biyu ya ganki sanda kike ɗaukar video ɗin nan, ko kuma ta cctv, dan Company kamar nasa dole asamu camaras tako ina”.         Idanu na waro sosai na matuƙar mamaki, Yaya Musaddiq ya jinjina min kai alamar tabbatarwa. “Samraah duk mai hankali dolene ya gane akwai dalilin Maash na amsa miki gayyatar da kikai masa cikin sauƙi. Dan bazai taɓa zama ya amsa miki bane kawai saboda kin jera masa tambayoyi. Kai ina dolene ma ya ganki fa, ya barki ne kawai bisa dalilinsa, sannan yazo a bainar jama'a ya amsa zaiyi hira dake, hakan na nufin akwai wani abu da yake ƙullawa”.          Sosai na zubama Yaya Musaddiq ido, dan tabbas zancensa yasa na fara dawowa cikin hankalina yanda ya kamata. (Humm you are vary smart girl) kalmar daya fara ambata a kaina kenan. Tabbas wannan mutumin terror ne na gasken-gaske. Shin mi yake ƙullawa? Dan dolen dole akwai abinda ke ransa kamar yanda Yaya Musaddiq ya faɗa. Kai ina buƙatar ganin ma program ɗin jiya gaskiya.....     “Kinga tashi muje, ba lokacin tunani bane yanzun”. Yaya Musaddiq ya faɗa cikin katse mun tunani. Miƙewa nai babu musu, dan basai na koma cikin gida ba dama....                🤙❤️🤙❤️🤙❤️    A ɓangaren Maash asubar fari ya farka, da ƙyar ya iya tashi saboda gaɓɓansa duk ciwo suke masa. Ruwa ya fara watsawa ya fito a gurguje ya kimtsa cikin wando da rigar polo. Koda ya fito su Hayatu suma har sun fito zasu wuce massalacin. A tare suka fita, bayan an idar da salla bai koma cikin gidan ba yace ma Tijjani ya fito da mota zasu je wani waje. Da sauri Tijjani ya shiga ciki, babu jimawa ya fito da mota, suma guards ɗinsa suka fito. Komai baice ba Hayatu ya buɗe masa baya ga shiga, shi kuma ya shiga gaba kusa da Tijjani. Jihar Jigawa suka nufa, a wani ƙauye dan akwai business ɗin da zai yi a wajen. Duk da dai da farko bai wani ɗauki abin da muhimmanci ba, sai da zasu je massalacin nan ne Hayatu ke sanar masa mutumin da zasuyi kasuwancin ya kira, kuma yana son suje da wuri ne.        Yinin ranar guda a Jigawa suka cinyesa. Ko abinci bai sakama cikinsa ba garama su su Hayatun. Sai Black tea kawai yake faman sha kasancewar duk inda yake yana tare da flaks ɗin ruwan zafinsa a mota, sai kuma chocolate dan mayenta ne da haɗaɗɗun biscuits. Sai bayan la'asar suka dawo cikin Kano a matuƙar gajiye. Musamman ma shi duk da dai yaci chocolate sosai amma yana buƙatar dafaffen abinci, dan rabonsa da dafaffen abinci sosai tun shekaran jiya a Lagos. Ko zama a falon baiyi ba ya wuce bedroom, suma dai su Hayatun duk a gajiye suke, dan haka kowa ya nufi sashensa danya watsa ruwa. Bathtub ya cika ra ruwan ɗumi sosai sannan ya shiga ciki, sai da yaji ko inansa ya miƙe sannan ya ɗauraye jikinsa ya fita. Duk yau sau ɗaya kawai yay waya da Ummien sa. Ji yake duk kewarta ta damesa. Sai dai yanzu yasan koya kira bazai samu ba dan ba lokacin kira bane dan sallar magrib aketa kira. Shiri yay tsaf cikin kaya marasa nauyi. Ya baɗe jikinsa da turare sannan ya saka slippers da ke ajiye yay ficewarsa.        Tun kafin ya ƙarasa fitowa cikin falon Hayatu dake zaune yana jiran fitowarsa ya miƙe da sauri. Dan tun ɗazun ya dawo daga wanka da yaje yayo shima a sashensa. Ya dawo ne da wuri akan batun cctv footage na jiya, dan yana ganin ya kamata su duba issue ɗin kar a samu matsala. Kallo ɗaya ya masa ya ɗauke kansa, sai kuma ya nufi ƙofa a taƙaice ya ce, “Kayi alwala”.        Cikin girmamawa Hayatu ya amsa da “Okay Sir”. Sai kuma ya saki murmushi yana mai binsa da kallo. A duniya boss ɗinsa da banne. Mutum ne mai abubuwan ban mamaki daban-daban. Ba kuma zaka tabbatar da hakan ba sai ka kasance a makusancinsa. ALLAH ya azurtashi da ni'imomi da yawa a rayuwa. Gadai ƙyawu kamar shine ya zana kansa. Ga dukiya, ga ilimin addini dana zamani. Yanada ƙyauta ga duk wanda ke tare da shi. Sai dai kuma hatsabibin kansa ne baifa mutunci a wasu fannin. Dan wani irin mutum ne a hagungunce da zaka iya ɗaukar lokaci baka fahimci alƙiblarsa ba. Ga taurin kam masifa da baƙar zuciya. Baya ragi ko ragowa ga duk ubanda yace masa kule. Yakan karya yatsar duk wanda ya nunashi dan baya ƙaunar raini. Shifa ko'akan business ana lallaɓa abokan harƙalla dan su dawo shi a garesa bai san wannan ba. Kana kawo masa hauka zai cireka a sabgarsa kawai. Sai dai baka isa tabbatar da waɗan nan halayyar tasa ba kai tsaye sai ka shigo gonarsa. Dan sumumu kasaune shi _*MACIJIN SARI KA NOƘE_*. A zahirinsa zaka ɗauka mutum ne mai sanyi da nuna halin ko'in kula, sai dai a kowanne motsi na cikin rayuwarsa a ankare yake. Domin indai brain ce ALLAH ya bashi. Irinsu ne ke juya akalar abubuwa a ƙanƙanin lokaci da kwanyarsu.....         Firgigit ya dawo hayyacinsa jin kiran sallah. Da sauri ya shiga toilet ɗin falon ya ɗauro alwala ya wuce masallacin shima...       Bayan idar da sallar isha'i suka shigo gidan. Sai dai Hayatu da Tijjani drivern sa sun rigashi shigowa. Dan su duka suna a gidan har baturiyar nan. Sai dai kowannensu yana a mabanbancin masauki da sai in shine ya buƙaci ganinsu zasu ganshin. Kusan mintuna goma suna a ƙaton compound ɗin gidan da ga jikin motoci suna hira sai gashi ya shigo shima. Ya ɗan dakata yay magana da masu gadi da suka kasance ƴan sanda har su uku sannan ya ƙaraso inda suke. Duk nutsuwa sukai kawunansu a ƙasa, baice da su komai ba ya wuce inda lafiyayyar ƙofar shiga sashensa take. Dan ta gilashi ce mai tsananin ƙyau da ɗaukar idon mai kallo. Gata golden daga waje sai walwali take kamar wani zinaren gaskiya. Da sauri Hayatu dake biye da shi ya buɗe masa ƙofar. Harararsa ya ɗan yi, Hayatu ɗin ya duƙar da kai ƙasa yana murmushi dan yasan laifinsa akan buɗe ƙofar ne tunda yana hanasu. Har ya shiga ya ɗan waiwayo. Driver dake ƙoƙarin komawa da baya ya dakatar ta hanyar faɗin, “Tijjani!”.      Da sauri Tijjani ya amsa masa da “Na'am ranka ya daɗe”.     Komai bai sake cewa ba ya cigaba da tafiyarsa ciki. Dan haka duk suka bisa. Duk da garin ba zafi ake ba, ba kuma sanyi ne mai tsanani ba dan ya fara bankwana falon a ƙanƙare yake da sanyin raɓar ac. Ga wani ƙamshi na musamman daya gaurayu da turarensa tamkar ba a jiya ne ya fara rayuwar cikin gidan ba. Zaune ya kai saman 3sitter. Kamar yanda ya saba zaman ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya yanzun ma hakan yayi. Shiru kamar mai nazarin wani abu sai kuma ya ɗago yana ma Hayatu nuni da remote dake a Centre table. Remote ɗin Hayatu ya ɗauka da sauri, dan ko ogansa bai magana ba yana saurin gane karatun shirunsa saboda da hakan ya horesu tun farko. Dan shi bamai yawan magana bane sai idan shine yaso hakan da kansa. Sai kuma idan yana a gaban mahaifiyarsa ko mahaifinsa, shima a wasu lokutan ne yake hakan, sai ko Ammie. Volume ɗin tvn ya sassauta tare da canja tasha zuwa inda yasan yafi yawan kallo a irin wannan lokacin. Tasha ce ta addini, sai dai suna gabatar da duka programs ɗin su ne da turanci, hatta da wa'azi kuwa........✍️          _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑬𝒊𝒈𝒉𝒕𝒆𝒆𝒏_ .......Gyaran murya ya ɗan yi idonsa akan Tijjani. Cikin sauri Tijjani da idonsa ke akan tv ya maido hankalinsa garesa. Kafin ma yace wani abu cikin muryar nan tashi kamar ta rowa ya taresa da faɗin, “Ina za'a samu abinci mai tsafta?”.        Cikin girmamawa Tijjani ya ce, “Ranka ya daɗe akwai gidajen abinci masu inganci dake tsaftace abincinsu sosai a garin Kano. Harma da masuyi a cikin gidaje sai dai kawai ai order suna da masu delivery da zasu iya kawo maka har inda kake, ko aje a amso”.        “Good. Sai ka samo duka gidan. Ka tambayi kowa abinda yake buƙata”      “In sha ALLAHU yanzu kuwa ranka ya daɗe”.    Bai sake cewa komai ba ya maida idonsa a television dan an fara gabatar da program ɗin da yay zaman kalla. Hayatu ne ya miƙawa TJ kuɗi masu yawa. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Nidai jallop rice da ƙirjin kaza nake so.”       Dariya TJ yayi ƙasa-ƙasa yana ƙumshe baki dan karta fito. Sai kuma yayma Hayatu nuni da ogan nasu da ido. Kai Hayatu ya jinjina masa yana sake gyara nutsuwarsa da maida hankalisa garesa ya ce, “Sir za'a karɓo maka kaima ko?”. Shiru kamar bazai tanka ba, dan yamayi biris tamkar baiji ba. Sai kuma batare da ya kallesu ba ya ɗan kalla agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa mai shegen ƙyau. Ya ɗan yamutsa fuska da jan siririn tsaki. “In dai bazai jima ba a samo min tuwon semo.. miyan kuka”. A tare suka amsa da girmamawa. TJ ya fita da hanzarinsa dan sun san baya cin abincin dare late, wani lokacin ma bai fiya ci ba. Yau ma suna ƙyautata zaton dan baici komai bane tun black tea ɗin safe. Haka yake abinci bai damesa ba, shiyyasa ga shi nan ko kaɗan baida wani tunbi, jikin ma badan yana haye-hayen waɗan nan tarkacen machines ɗin na motsa jikin zamani ba da zai kasance ne falen-felan. TJ na ficewa Hayatu ya katse tunaninsa tare da matsowa inda yake. Da ga tsayen da yake kamar soja ya ɗan rissina yana fito da flash da ga aljihunsa da faɗin, “Sir ga cctv footage ɗin an samo”. Juyowa yay ya ɗan kalli Hayatu ɗin a yanayin jin daɗin hakan. Sai dai kuma ko kaɗan fuskarsa bata nuna komai ba tana nan a ɗaurenta tamau. Kujera ya nunama Hayatu. Zama yay yana ɗaukar laptop dake a Centre table ajiye ya saka flash ɗin jiki. Kafin ya miƙe yaje har gabansa batare da yayi playing video ɗin ba. Ajiye masa yay a stool ɗin daya jawo a hankali gabansa sosai. Sannan ya zauna a saman carpet kusa da ƙafafunsa yana shiga inda folders ɗin videon suke. Duk zubama screen ɗin laptop ɗin ido sukai. Cikin ƙwarewar aiki Hayatu ya zaluƙo video ɗin sashen da abin ya faru, tare da dai-daita lokacin da komai ya faru sai dai baiyi playing ba ya ɗan ɗago ya kallesa.          A hankali ya furta, “Kunna”.     Kunnawar yayi. Ko'ina ya fara nuna shiru babu kowa babu motsin komai. Kusan minti ɗaya da wasu sakanni sai ga Samraah na bubbuɗe ƙofifi bayan ta fito da ga wani lungu da suka san restrooms na ma'aikatane a wajen. Yanda take taɓa ƙofofin tana ɓata fuska kamar zatai kuka zai baka tabbacin ta ɓata ne. Can cikin takaici ta fincike face mask ɗin fuskarta. Ƙyaƙyƙyawar fuskarta da babu zanen komai na kwalliya ta bayyana. Hayatu dai ya gagara haƙuri sai da ya furta “Masha ALLAH” a hankali. Dan ko makaho ya laluba fuskar Samraah yasan yarinyar ƙyaƙyƙyawa ce, duk dama eyeglasses ɗinta har lokacin yana a idanunta shi bata cire ba. Isowarta ƙofar da suke ciki ya sanya Hayatu waro idanu sosai, sai dai bai iya cewa komai ba. Ta buɗe ta ɗan leƙa. Sai kuma tai baya a rikice alamar akwai abinda ta gani. Wayarta data zaro tai danne-danne ta kanga tabbacin video take musu yasa Hayatu kasa haƙuri ya furta, “What! Sir itace kenan?”.        Bai samu amsa ba, dan ogan nasa ko motsi baiyi ba har sai da ya kai ƙarshe. Fitowarsa, tsintar nurse mask. Har cigaba da video da Samraah tayi sanda suke fita da gawar mutumin. Cikin ƙanƙanin lokaci Hayatu ya gama haɗa uban gumi kamar wanda ke a filin kokawa. Shi kam duk da a birkice take video ɗin yaga matuƙar ƙarfin halin yarinyar nan. Motsin da ogansa yayi yasa hankalinsa dawowa jikinsa. Ya ɗan ɗago ya kallesa. Sai da gabansa ya faɗi ganin yanda cat eyes ɗinsa suka canja launi. Dan gaba ɗaya gwaiduwar tsakkiya ta ɓace ta zama ƴar siririya exactly yanda na mage suke komawa idan suna a cikin haske. Batare da ko kallon Umar ɗin ya sake yi ba ya miƙe ya fara tafiya. Sai da yaje gab da ƙofar bedroom ɗinsa sannan cikin dakiyar muryar dake tabbatar da ransa a ɓace yake ya furta, “A nemota duk inda take. A cigaba da bin duk wani motsinta daga nan zuwa sati biyu”.         “An gama Sir. Amma in baka manta ba ka bata damar yin hira da kai ma”. Hayatu ya faɗa cikin tsumar jiki. Cak ya tsaya daga ƙoƙarin shigewa da yake yi kamar mai nazari, sai kuma batare da ya juyo ba ya furta “Zanyi tunani akan hakan”. Buɗe baki Hayatu yay zai sake magana cikin nuna gamsuwa, sai dai harma ya riga yay shigewarsa shi. Hayatu ya rabga tagumi tare da faɗin, “Tab ƙyaƙyƙyawa kin shiga uku wlhy, bama ke ba duk zuri'arki kin sakasu a masifa. Ke miya kaiki shiga gonar da bataki ba. Aikata wannan aikin da ba'a sakaki ba, karanbaninki ya ɗebeki shiga fadar sarkin aljanu. Dan oga ALJANI ne irin ifiritan nan.” yana cikin wannan sambatun nasa TJ ya shigo da ledoji masu ƙyau an musu tambarin gidan abinci. Firgigit Hayatu ya dawo hayyacinsa tare da gyara yanayinsa. TJ da ma bai wani lura da halin da yake a ciki ba ya ajiye masa tasa ledar sannan ya ajiye wata a Centre table yana faɗin, “Wannan tuwon oga ne. Shi na tsaya ma sai da akayisa yanzu-yanzu gashi nan da zafinsa yanda zai masa daɗin ci.”         “Ai wannan tuwon mawuyacine ya samu shiga kuma yanzu”.     Idanu TJ ya waro a rikice ya furta, “Na shigangaɗi Hayatu badai na makara ba? Wlhy babu tuwonne amma matar tace zatayi da sauri tana da miya. Ni kuma naga tunda yace yana buƙatarsa yana so ne shiyyasa nace tayi da sauri...”       “Kai ka kwantar da hankalinka badan ka daɗe bane ba kawai dai wani abunne daban ya ɓata masa rai. Amma bari na gwada faɗa masa ka dawo mugani”.      Ajiyar zuciya TJ ya saki, duk da kuwa yanayinsa bai warware ba. Dan in har ogan nasu na cikin ɓacin rai ko damuwa suma sukan shiga matuka saboda yanda suka ɗauki al'amarinsa da matuƙar muhimmanci a rayuwarsu. Tashi Hayatu yay ya nufi hanyar bedroom ɗin nasa, sai da yay jimm a tsaye bakin ƙofar kafin yay knocking a ɗarare. Ko motsi ba'aiba, bai gajiyaba ya sake yi tare da sallama. Nan ma anja kusan minti ɗaya kafin ya amsa masa a daƙile. Sake nutsuwa Hayatu yay kafin cikin dauriya ya ce, “Kayi haƙuri Sir, dama TJ ne ya dawo, a kawo maka abincin nan ne”.         “No! I'm okay”.     Shiru Hayatu yay cikin nuna damuwa ƙarara a fuskarsa. Sai kuma ya sake raunana murya ya ce, “Please Sir, duk yau fa bakaci komai ba. Ko nace ma rabonka da abinci tun shekaran jiya a Lagos. Abu mafi saka Ummie damuwa a rayuwa shine ka kwana da yunwa. Dan ALLAH ko kaɗanne ka daure kaci, saboda nasan duk da bata tare damu zata ji a jikinta kamar yanda ta saba”.       Wani irin cizar lips yay da ga zaunen da yake a bakin gadon hannunsa dafe da kansa. Hayatu ya matuƙar sanin lagonsa a rayuwa. Dan shine kaɗai yake iya bi da shi fiye da kowa bayan mahaifiyarsa. Hakan kuma nada alaƙa da sanin da yay masa tun ƙuruciya. Duk da dai shi ya girmi Hayatun da kusan shekara biyar ma, amma kasancewar sun tashi ne shi da iyayensa a cikin gidan kakansa da ya haifi Ummien sa yasa yay masa farin sani na gaske. Ya jima a gurin kamar bazai motsa ba sai kuma a daƙile ya furta, “Kawo nan”. Cikin sauri Hayatu yabar jikin ƙofar cike da farin ciki bawan ALLAHn kamar cikinsa zai kai. Babu jimawa kuwa sai gashi da tuwon. A can ya shirya masa shi saman table ɗin gaban sofa dake bedroom ɗin, har lokacin kuma yana a zaune bakin gadonsa hannunsa dafe da kansa. Yanayi ne dake nuna yana cikin zafin rai, dan Hayatu ya sanshi a rayuwa fiye da tunanin mai tunani. Ganin Hayatu ɗin baida niyyar fita yaja siririn tsaki yana ɗagowa, harararsa yayi da faɗin, “Ka tsaya gadi na ne sai naci ka gani?”.          Ƙasa Umar yayi da kai yana ɗan murmushi. Sai kuma ya rissina tare da faɗin, “Ayi haƙuri Sir”. Daga haka ya fice a ɗakin. Wani tsakin ya sake ja sannan ya miƙe zuwa gaban sofa ɗin ya zauna. Hatta ruwan wanke hannu Hayatu ya tanadar masa. A nutsensa cikin yanayinsa na rashin gaggawa akan komai ya fara cin tuwon dan yana son tuwo sosai saboda fevorite food ɗin Ummien sa ne, ada sanda yana yaro idan tayi tace sai yaci yakan zauna yayta kuka shi bazaici miyan daddawa mai wari ba. Amma bayan wani lokaci da rayuwa ta canja kanta zuwa abinda bai taɓa mafarkin riska ba a cikinta sai ya maida tuwon fovorite nashi shima. Yaci kusan rabin malmala ɗaya ya ajiye duk da kuwa tuwon ya masa matuƙar daɗi,  sai dai bai cika son cin abinci late haka ba. Shiru ya ɗan yi zaune a wajen kafin ya tashi zuwa toilet. Brush yayi da sake gyara jikinsa ya fito. Ya samu Hayatu har ya shigo ya tattare komai harda sakama ɗakin freshener ya ƙara dai-daita masa ac. Komai baice ba ya rage kayansa zuwa na barci, sai dai maimakon kwanciyar zama ya sake yi a sofar yana ƙoƙarin kunna laptop ɗinsa, dan yana son ƙarasa harƙallar wani business ɗinsa kafin ya kwanta. Dai dai kuma mi hakan kamar neman gagararsa yake. Dan tunda ya kunna ya gagara danna ko keyboard ɗaya tunaninsa ma neman tafiya yake wani sashe daban. Da ga ƙarshe dai ya ture laptop ɗin gefe ya ɗauki wayarsa. Wata number da aka saka Dude ya nemo tare da danna kira.......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑵𝒊𝒏𝒆𝒕𝒆𝒆𝒏_ ......Kusan lokaci ɗaya muka iso garejin da Mansoor. Dan haka babu ɓata lokaci muka nufi cikin motarsa, dan nan ɗin zaifi mana zama sirri fiye da ko'ina saboda abinda zamu tattauna ɗin. Gaba Yaya Musaddiq ya shiga ni kuma baya. Sun gaisa da Mansoor cikin mutunta juna kamar yanda suka saba nima na gaishesa. Amsawa yay idanunsa a kaina ta cikin mirror.        “Ya kamata ki huta da kukan nan Samraah. Sai kace kece kika aikata laifin nan. Kinga kuwa yanda idanunki suka koɗe”. Mansoor ne yay maganar cikin nuna damuwa matuƙa. Yaya Musaddiq dake saurarensa ya ce, “Ai ita haka take bata bin al'amarin rayuwa a hankali ka ganta nan. So take sai ta jama kanta wani ciwon muma ta sake sakamu a wata damuwar sannan”.      Idanuna na cikowa da hawaye na ce, “Kuyi haƙuri Yaya ba haka bane. Wlhy na kasa mantawane da ganin gawar kawai. Amma in sha ALLAHU bazan ƙara ba”.     “ALLAH yasa hakan” Yaya Musaddiq ya faɗa. Yayinda Mansoor yaja numfashi ya fesar tare da amsawa da Amin. Idanuna na share tare da ƙoƙarin yin magana wayar Mansoor ta shiga ruri. Tamkar an saita sai tawama ta fara. Kusan a lokaci ɗaya duk muka kai hannu domin ɗauka. Sai kuma muka kalli juna tare da sake ɗagowa duk muka kalli Yaya dake tambayar mu “Lafiya kuwa?”.         “Daga office ne”. Mansoor ya bashi amsa yana ƙoƙarin kai wayar kunnesa. Nima dai tuni nakai tawa tare da yin sallama. MD ne ya amsa daga can, batare daya bi takan gaisuwata ba ya ce, “I'am Sorry Samraah muna son ganinki a office yanzu Please”.       “Yallaɓai lafiya kuwa?”. Na faɗa da sauri hankali a ɗan tashe.      Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce, “Kinga kwantar da hankalinki ba wata damuwa bace. Mun samu baƙuncin babban baƙone mai matuƙar muhimmanci da muka daɗe muna fata. Ya kuma ce da ke kaɗai yake son ayi hira da shi”.          “Ni kuma oga? Duk mutanen dake a gidan sai yace sai ni. Wanene haka da ƙarfin halin nan? Sai kace wani abin cin rabo. Ya kamata Ku faɗa masa ba sashin da nake aiki ba kenan”.       “Humm Samraah Please mana. Dan ALLAH ki shirya kawai ga driver na nan ma na aiko gidanku ya ɗaukeki a motata”.     Sake tashi hankalina yayi, sai dai kafin nayi magana oga ya yanke kiran. Sagale nai kawai ina kallon wayar kamar wata gunki. Wane irin baƙone da zai tada hankalin oga har haka. Sannan kuma ma yace ni yake so nai hira da shi. “Kodai mutumin nan ne?”. Na faɗa a zahiri batare da nasan maganar ta suɓuce min ba. Atare Yaya Musaddiq da Mansoor da shima yay zororo alamar kiran da akai masa nada nasaba da nawan suka juyo suna kallona.      Yaya Musaddiq ne yay ƙarfin halin cewa “Wane mutumi?”. Firgigit na dawo hayyacina. Dan na fahimci zancen zucini ne ya fito fili. Idanuna ne suka cicciko da ƙwalla. Cikin rawar murya na zayyane musu komai da MD yace min. Mansoor ne yay saurin faɗin “Tabbas akwai alamar tambaya. Dan nima akan abinda suka kirani kenan. Amma ina ganin ki kwantar da hankalinki bari muƙarasa office ɗin domin ganin wanene ɗin ko kuwa Yaya Musaddiq?”.          “Tabbas shawararka yayi Mansoor. Tunda akan aikine bai kamata ayi sakaciba kam. Kuje idan kun dawo ma ƙarasa maganar in sha ALLAH. Nima zuwa lokacin na ɗan ƙara yin nazari.”     Mansoor ne kawai ya iya amsa masa. Nikam sai binsu da kallo kawai nakeyi. Yaya Musaddiq ya fita yana buɗe baya yace na fito na dawo gaban. Ganin banda niyyar hakan ya buɗe ya kamo hannuna ya fiddoni ya maida gaban. Key kawai Mansoor yayma motar ya haura kan titi. Babu wanda ya iya sake yin magana a cikinmu. Kafin mu isa office ɗin kuma sai danno mana kira MD yake yana kuma sakawa amana. Da wasu kalar shegun zuƙa-zuƙan motoci na alfarma muka fara cin karo a harabar gidan. Sai mutane cikin baƙaƙen kaya tsatstsaye ƙiƙam kamar masu tsaron ƴan fashi. Mudai wucesu mukai muka shiga abinmu. Duk da lahadine mun samu ma'aikatanmu dake duty a wannan ranar dukansu. Harma da wadanda aka kira irinmu da ranar suna hutu suma kamar mu ɗin dai. Office ɗin MD muka wuce kamar yanda aka sanar damu yace muyi. Anan ɗin ma mun tadda mutane biyu irin waɗanda ke a haraba su biyu a jikin ƙofar. Matsa mana sukai muka shiga bayan Mansoor yayi knocking an bamu izinin shiga. Mun fara cin karo da ƙamshin turare mai armashi sosai. Sai sanyin ac a office ɗin kamar ba safiya ba. Wannan kuma ba halin MD bane zama cikin ac da ƙarfi haka.         Akan MD idanunmu suka fara sauka. Kafin dattijon dake zaune a kujerar kusa da shi cikin shigar ɗanyar shadda mai tsananin ƙyau da ɗaukar hankali sai maiƙo take da walwali. Ƙyaƙyƙyawane sosai baƙi ga dogon hanci da shiryayyen farin gashinsa daya ƙawata taswurar fuskar tasa. Gaishesa muka farayi kawunanmu a ƙasa. Dan tun shigowarmu ya zuba mana idanunsa manya farare yana murmushin bajinta. Yanzun ma da fara'ar ya amsa mana. Sai kuma ya kalla MD ɗin yana faɗin, “Inaga idan kun shirya mu fara abinda ya kawomu kawai. Dan na faɗa maka zanbi jirgin ƙarfe biyu ne domin komawa Lagos, ina kuma da wasu uzirin bayan wannan. Gashi yanzu 10:30.”        “Hakane ranka ya daɗe” MD ya faɗa cike da tsantsar girmamawa ga dattijon. A karo na farko muka kalla juna ni da Mansoor. Sai kuma muka maida kan MD da yay kiran sunanmu a tare. Idonsa akan Mansoor ya ce, “Mansoor ka duba tare da tabbatar komai yayi dai-dai a can ɗin. Muma gamu nan fitowa.”        Amsa masa Mansoor yay cikin nuna ƙaulani, sai dai baice komai ba ya juya ya fita. MD ya maido da idanunsa kaina yana miƙamin takardun hannunsa. “Ke kuma Samraah ga wannan. Sune tambayoyin da zakiyi, ki ɗan dubasu ko. Sai kuma ya kamata kije ki gyara makeup naki kema gamu nan fitowa.”         Ɗan jimm nayi kamar bazan amshi takardar ba, MD ya wani marairaice fuska tamkar zai fasa ihu cikin nuna alamar roƙona da idanu. Jinai kamar na balla masa harara. Amma dai na daure na amsa takardun kawai ina faɗin, “Okay Sir” a hankali. Ina daga tsayen na dudduba komai, batare da nace komai ba na ajiye masa a saman tebir ɗin. Sannan na juya na fita. Da ga shi har baƙon nasa ina jin idanunsu a kaina. Da ƙyar na iya ficewa zuciyata na ƙara nauyi ga mamaki da cushewar kai na rashin iya gane komai a wannan al'amari. Dan magana ta gaskiya duka tambayoyin da MD yace sune zan masam sun matuƙar bani mamaki. Na kuma sake tabbatar da lallai akwai wata a ƙasa. Watan da shi kansa MD idan yay wasa sai ya zurma ciki ƙwarai da gaske....        “Tofa, mi kuke tunani masu karatu🤥? Nima fa kamar na shiga ƙaulanin ne🤔”.      ✨・o・✨・o・✨・o・✨            Sosai yasha barci mai lafiya a safiyar ta yau kasancewar a daren jiya ya jima bai kwanta ba. Dan tunda ya dawo massalaci sallar asuba da Ummiensa kawai yayi waya ya sake komawa ya kwanta. Bai tashi ba sai yanzu babu jimawa. Wanka kawai yayi tare da gyara jikinsa cikin wando 3quater mai laushi kalar baƙi da rigarsa fara da adon baƙi kaɗan itama mai laushi. Dogon hannune da ita tare da hula. Sai dai ya saki hular a bayansa, sannan bai saka zip ɗin rigar ba. Hakan ya bama farar singlate ɗinsa damar fitowa sosai tare da ɗamammen cikinsa da har kana iya ganin kwanciyar gurayen kansa dake nuna shi matsayin mutum mai tsananin motsa jiki. Yau dai bai ɗaure gashin ba, sai dai yasha gyara sosai dan daga shi har siririn kwantaccen sagensa sai uban ƙyalli da ƙamshi sukeyi. Ga gashin ya ɗan sakko masa har kafaɗa kaɗan. Magana ta gaskiya babu wanda zai kalla bawan ALLAHn nan ya yarda wai ya haɗa jini da baƙaƙen fata. Dan sam baya kammani da su sai dai fatarsa da tai ɗan diff ba kamar na fararen dake kasancewa jazur ko fari fat ba. Amma shi yanayin da fatar tasa take ma sai ya ƙara masa wani ƙyawu na musamman. Kai tsaye ga coffee machine ɗin sa da ke a falon ya nufa. Cikin mintina kaɗan ya haɗa coffee. Ƙyaƙyƙyawan mug ɗinsa na zallar farin glass ya ɗauka ya tsiyaya fin rabi a ciki. Sannan ya tako a hankali yana kaiwa bakinsa zuwa cikin falon sosai. Furucin daya fito daga cikin television dake aiki a falon ya sashi karkata hankalinsa ga tvn. Dai-dai nan Hayatu ya shigo kamar wanda aka koro. Kaɗan ya juyo ya kallesa cikin yanayin nan nasa na rashin sakewa, sai kuma ya sake maida kansa ga tvn yana sake kai mug ɗin kan ɗan ƙaramin bakinsa ya zuƙi coffee ɗin duk da zafin da yake da shi.         Hayatu da gaba ɗaya hankalinsa ke a tashe ya ce, “Sir kaga abinda ke faruwa kuw......” sauran maganar ta maƙale sakamakon saukar idonsa akan tvn shima. Da sauri ya ɗan yi baya kamar wanda ke shirin faɗuwa. Ya dai samu nasarar dafe hannun kujerar dake kusa da shi yana bin ogan nasa da ya ƙarasa ya zauna cikin kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya da kallo. Yasan halinsa sarai akan dakiyar masifa dayin biris da abu kamar bai damar ba. Amma magana ta gaskiya wannan bai kamata ai biris ba. Zama yay ya samarwa kansa nutsuwa. Kafin ya furta, “Amma Sir mizai sa Baba prof.. zuwa Kano a yau har yayi hira da yarinyar nan ne? Kodai ya amince da batun buɗe companyn yanzu? Wlhy ni du kaina ya kulle ma”.........✍️ _Ni ma dai mai ɗaukar rahoton neman ruɗar fani ɗin kuke Hayatu PA.🤥🤔_      _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚_ .......Kamar yanda Hayatu yasan bazaice komai ba baice ɗin ba kuwa. Sai ma aikin shan coffee ɗinsa da yake hankali kwance idanun nasa dai a tvn dan har an fara program ɗin. Gaba ɗaya hirar anyita ne akan abinda ya shafi harkar ilimi a Nigeria. Da rawar da su malamai ɗin suke takawa domin ganin matarbar ilimin ta dawo hayyacinta da ga mutuwar tsayen da tayi musamman daya kasance tun daga tushene. Dan yanzu secondary schools tafi kowace gaɓa lalacewa a harkar karatu, in ba makarantar kuɗi zaka kai yaranka ba sai a hankali. Gashi kuma Sakandire ɗin nan ne ake ganin tamkar mahaɗar dake riƙe da kowanne reshen ilimin dan anan ne ake karatu tuƙuru cikin halin ƙuruciya da babu wasu damuwoyin fara fuskantar ƙalubalen rayuwa irin na girma. Wannan hira ta matuƙar ɗaukar hankalin mutane, inda ta haifar da cecekuce sosai tare da yaba ma prof... ɗin. Dan tun kafin a kammalata saƙwanni sun cika kowane dandalin sada zumunta na wannan gidan tv da rediyo. Yayinda wasu ke tattaunawa a dandilansu na sada zumunta. A cikin awa ɗaya da akai da Prof.. K/Mashi an amsa harda wayoyin mutane, ya kuma bada cikakkun amsoshi masu jan hankali da suka sake birge mutane da ganin kimarsa da girmansa. Duk da a baya ana zaginsa akan yanda yake aiki tuƙuru ma kudancin Najeriya ɗin kasancewarsa mazaunin can shi da gaba ɗaya zuri'arsa. Dan wasu na ganin a komai nasa bama ya alaƙanta kansa da arewa sam, tamkar ma baida wani alaƙar dasu, musamman idan yana sukar ƴan siyasar arewan da ƙalubalantar shuwagabannin yankin.          Koda aka kammala ma babu alamar Maash zaice wani abu. Zuwa yanzu dai kansa na jingine da kujerar idanunsa a lumshe. Ta ƙasan ido Hayatu ke kallonsa da nazartarsa. Sai kuma a hankali ya furta, “Sir miza'a kawo maka breakfast?”.       Shiru babu alamar zaima motsa balle ya tanka masa. Sai kuma dai cikin motsa lips da ƙyar ya furta, “Waka ɗora akan aikin bincike akan yarinyar nan?”.            Ƙasa Hayatu yay da kansa, cikin girmamawa sosai ya amsa da, “Da kaina nayi Sir. Dama abinda nazo kawo maka kenan. Sai kuma wanda zai ringa bibiyar tata ne kuma ina kan nazari. In sha ALLAHU daga nan zuwa yamma zan kawoshi shima.”     Yana daga kwancen ya ɗan buɗe idanunsa yana kallonsa. Hayatu ya ƙara rissinar da kansa yana ɗan murmushi, dan yasan abinda yay ɗin ya faranta ran ogan nasa koda bai fito ta faɗa ba. Ci gaba yay da faɗin, “Sunanta Samraah Abdul-wahab Gwarzo. Wasu kan kirata Sam-G. Tana da yaya Musaddiq da ƙani Hafizzullah. Musaddiq ɗin makanike ne, shike riƙe da rayuwarsu, ƙanin nata kuma na jami'ar Umaru Musa Yar'adua dake Katsina yana karatu. Iyayensu sun jima da rasuwa, a hannun Uncle ɗinsu suke tun suna ƙanana. Akwai wani yaro Mansoor da ko yaushe suna tare shine zata aura dan har maganar iyaye ta shiga. A zahiri Samraah bata da hayaniya ba kuma sabgar kowa take shigaba sai in itace taso hakan. Sai dai kuma tana da tsiwa a wasu lokutan musamman ga wanda ya shigar mata hanci. A shekarun baya kaɗan ta fara rubuce-rubuce kan abubuwa masu muhimmanci musamman da suka shafi ƙananun yara mata dake tallace-tallace a tituna. Sai dai tunda ta fara wannan aikin ta ɗan rage hakan. Bincikena kuma ya tabbatar min tanada fans sosai, dan a duka shafukanta akwai fallowers dake fallowing ɗinta sosai. Na tabbatar da yanda suke jin daɗin karatun rubuce-rubucen nata ne ta hanyar comments da suke mata. A office kuwa tana fannin ƙananun ma'aikata ne. A ɓangaren rediyo ta fara aiki kuma. Sai dai ƙwazonta da yanda program ɗin data bada shawarar samarwa akan matasa ya amsu, ya saka suka maidata itace mai gabatar da program ɗin. Da kuma a iya rediyo kawai akeyinsa, amma yanayin karɓuwarsa yasa suka koma gabatar da shi har da television, sannan shi MD ɗin su ne ya bata power sosai a al'amarin. Shiyyasa ma ake zargin yana sonta ne duk da yasan akwai alaƙa mai ƙarfi tsakaninta da shi wancan yaron Mansoor, amma har yanzu bai san iyayensa sunje gidansu ba ma har anyi maganar aure.” ɗan matsawa yay gabansa yana yunƙurin ajiye tab.. ɗin dake a hannunsa yana cigaba da faɗin, “Nayi fallowing duka shafukanta, gashi ko zaka duba”.         Hayatun ya ɗan kalla sai kuma ya ɗauke idanun nasa. A daƙile ya ce, “Ba buƙata. Ka kammala komai dan zuwa jibi maybe zamu wuce. Ka tura ma MD nasu takardar amsa gayyatar da tai min, sai dai kar ya wuce gobe” daga haka ya miƙe. Har ya shige bedroom ɗin sa Hayatu da kansa ke ƙasa na binsa da kallo. Sai kuma yaja numfashi tare da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi yana kaiwa zaune cikin lallausar kujerar dake a falon. Tagumi ya zuba da hannaye biyu, gefe ɗaya mamakin komai yake yi, wani gefe kuma na ayyana masa akwai abinda ogan nasa ke shiryawa. Kuma tabbas da wahala ace zai kasance mai daɗi, yana tausayin yarinyar nan, dan ta taroma kanta match. Bashi da zaɓin daya wuce cika umarni, dan haka ya ɗauka tab.. ɗinsa. A take yay kiran wani tare da buƙatar number ɗin MD na gidan tvn na AlHERI. Ko mintuna biyar ba'a cikaba kuwa sai ga saƙon Number ɗin ya shigo masa. A take ta shirya text message ya tura musu kamar yanda Maash ya umarcesan.....     Yayanmu nima fa ka fara ban olo gaskiya😌🥺🥺.       🌟(☉。☉)!(☉。☉)!(☉。☉)🌟                     Sam nutsuwa bata ɗan dawo jikina ba sai da aka kammala duka program ɗin. Bayan an ɗauke camara daga kanmu na sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi ina mai lumshe ido. Ɗan kallona prof.. yay a kaikaice sai kuma yay ɗan murmushin manya yana miƙewa. Yana fita a ɗakin shi da MD sauran ƴan uwana ma'aikata sukayo kaina. Ruwa aka fara bani nasha, na sake samun nutsuwa sannan nima na miƙe. Muna daga harabar gidan ni da Mansoor dake lallaɓani muje muci abinci aka aiko kiranmu. Dole cikin muka koma. Inda muka samu dukkan ma'aikatan da suka bada gudunmawa a program ɗin har ƴan bayan fage a office ɗin MD. Zama mukayi kamar kowa muma. Daga haka Prof.. ya fara mana bayanin godiya, tare da sanar mana dalilinsa na gabatar da wannan program ɗin cikin gaggawa haka. Sosai muka nuna gamsuwarmu. Musamman ma ni da kaina duk ke a ɗaure da farko. Ƙyauta dukanmu ya danƙa ma kowa a envelope ɗinsa. Daga haka yay mana godiya muma muna masa. Sai dai me ni sam hankalina ya gagara tsayawa waje guda akan hakan. Kallo na fara bin sauran ƴan uwana da shi, kafin na miƙe zaram kamar wadda akaima allura nabi bayansa da sauri. Mansoor na ƙoƙarin tsaidani da son jin ina zanje bamma sauraresa ba na fice da sassarfa. Isowata yayi dai-dai da buɗema prof.. mota zai shiga. Ga mutanensa zagaye da shi kamar zasu iya hana mutuwa ɗaukarsa. Amma ko'a jikina nai sallama kaina tsaye. Su duka juyowa sukai suna kallonna musamman MD da yay rakkiya tare da Prof....         Fuska ɗauke da murmushi Prof.. ya ce, “A'a ɗiyata ko kinyi mantuwa ne?”.     Ƙasa nai da kaina ina ɗan murmushin ƙarfin hali. Kafin cikin ladabi da dakiyata na ce, “A'a ranka ya daɗe. Dama uhm....” sai kuma nai shiru na kasa cigaba da faɗa ganin yanda suka tsatstsareni da idanu su duka. Murmushi mai sauti Prof... yayi yana sakin murfin motar ya juyi gareni da ƙyau. “Daughter yi maganarki ƙofa a buɗe take ai. Ko mu koma gefe ne?”.      Da sauri na ce, “A'a Sir ba sai munje ko'ina ba. Mun gode sosai da karamcinka garemu, amma dan ALLAH kayi haƙuri zan dawo da wannan dan ana biyana albashi akan aikina, kuma yana wadatar dani”.       Bashi ba hatta MD ina ganin yanda yay wani irin sororo yana kallona. Ni dai na ɗauke kaina ina miƙama yaronsa daya raba mana envelope ɗin. Ganin ya tsaya yana kallona bashi da niyyar amsa na ɗaura masa kan kayan hannunsa na juya a nutse na bar wajen. Ina jin yanda idanunsu sukai min riiiii aka. Amma ban waiwayo ba. Cin karo muka kusan yi da Mansoor da alamu suka nuna biyoni yayi. Na ɗan ja da baya ina faɗin, “Ya salam I'm sorry ban san ka taho bane”.         “Babu damuwa” ya faɗa yana kallon hannuna. Fahimtar hakan yasa kai tsaye nace masa “Na mayar musu ne?”.      “Mi ɗin?”.    Ya faɗa cikin waro idanunsa sosai waje. Bakina da ke cikin face mask na tura gaba da faɗin, “Yo abinda suka bamu. Ni gaskiya bana ra'ayi dan zuciyata sam bata ma kwanta waje ɗaya ba. Ta yaya mutum zai taso rana tsaka ya ce muyi hira da shi babu wani goron gayyata babu notes sannan ya kuma kawo wani abu ya bamu wai matsayin ƙyauta. Dan ALLAH kai baka ji abin banbarakwai ba? Shine fa wanda kwanaki akaita kace-nace ɗin nan akansa game da abinda ya faɗa akan shugabannin arewa. Gashi kuma da bakinsa ya faɗa shi haifaffen jihar Kano ne. Amma bai ragi balle ragowa wajen sukar mana mutane kamar wani maƙiyinmu”.        Idanu kawai Mansoor ya zuba min kamar mai nazari. Ya buɗe baki zaiyi magana sai ga MD ya iso kamar a fusace. Dan cikin yanayi kamar faɗa-faɗa ya ce, “Samraah sameni a office”.         Sai da na taɓe bakina dake a cikin face mask sannan na amsa masa da to ciki-ciki. Yana juya baya kuma na bisa da harara. Ƙin tafiya nai har sai da Mansoor ya mun magana. Batare da shima na tanka masa ba na wuce fuu nabi bayansa........✍️ *_“Amma Samraah miyyasa kika ƙi amsa bayan kuma kema kin gamsu da bayanin da yay muku na dalilin hirar? Sannan kin siffantashi da mutane kirki a halittar jiki da yanayinsa, kuma bayanansa sunja hankalin mutane da yawa a yau ɗin har hakan ya sake ɗaga darajar gidan tvn ku?”._* _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚-𝑶𝒏𝒆_ .......Humm Bily a zahirance banda wani dalilin yin hakan kamar yanda kowa zai iya gani ko fahimta. Sai dai ni a ƙasan zuciyata ina jin dole-dolene bai kamata na amsa koma miye ɗin ba. Dan babu dalilin hakan bisa hujjoji da dama. Amma ban sani ba ko kema zaki iya fahimtar hujjar tawa a yanzu. Ko kuma sai anan gaba cikin abinda zai zo a labarin nan nawa. Dan a yanzu kam tabbas babu wani dalilin da nima zan tilasta miki gamsuwa dani. Amma dai muje zuwa ofishin MD dake kirana.      (Babu musu na jinjina mata kai, amma magana ta gaskiya al'amarin wannan Sam-G ɗin taku yana ɗan rikitani. A ido zaka iya mata kallon like innocent people. Sai dai a ɗan zaman da nai da ita na fahimci taƙadarar kanta ce. Sannan akwai taurin kai yana jinjirin jaki. Kar dai na cikaku da zance ku muje zuwa dan jin yaya ta kaya a offishin MD)        Tsaye na samesa yana faman kai kawo a tsakkiyar office ɗin nashi. Sai faman furzar da huci yake kamar wani bajimin rago. Ko ɗar banji ba a raina na rafka sallamata. Juyowa yay yana kallona da idanunsa da suka kaɗa sosai. Kamar wanda ke shirin dukana ya wani zaburo kaina har sai da na ɗan ja da baya ina waro manyan idanuna waje.        “Samraah kin san mi kikayi kuwa? Kin san wanene wannan mutumin kuwa? Kin san ƙyautar mi ya baki kuwa? Amma kika watsa masa ƙasa a ido ta hanyar maida masa bayan ya fifitaki sama da kowa. Kuɗi duk ya bama sauran 50-50k, amma ke makullin mota ya baki batare da ko dubawa kinyi ba kika ɗauka kika maida masa...”         “Mata fa dai?”. Na tambaya da iya gaskiya ta. Shima cike da ƙwarin gwiwa ya amsa min da “Yes Mota Samraah. Shiyyasa a kullum nake faɗa miki ke ɗin mai sa'a ce dear”. Kaina na ɗan girgiza da murmushin basarwa, na ce, “Humm to amma Sir mi zanyi da shi idan na riƙe? Sannan wace amsa zan bama iyayena idan sun tambayen a ina na samu mota? A shi karan kansa mi ma zaisa ya mana irin wannan ƙyautar haka dan kawai munyi hira da shi?”.       “Tab ɗin, wlhy yarinyar nan baki da hankali...” ya faɗa cikin ƙunar rai, a take na sake tamke fuskata dan kalmar tasa ta mun matuƙar zafi a zuciya. Duk yanda naso na shanye na gagara hakan, kai tsaye nace masa, “Sir minene abin rashin hankali anan? Bayan kuma na faɗa maka hujjata. Wannan fa rayuwata ce”          Wani irin tsayawa yay duka hannayensa riƙe da ƙugunsa kawai yana kallona tamkar ya samu television. Ni kam na sake fuskewa kamar ban san yanayi ba. Na fahimci takaicina ne ya maƙureshi ya hana shi cigaba da magana. Dan a fusace ya sa ƙafa ya tunkuɓar da flower base ɗin da akai ado da ita a office ɗin, sannan ya ce, “Samraah out. Get out of my office now..”       Ko kallonsa banyi ba na juya nai ficewata. In ma ca yay na bar Company ɗin gaba ɗaya daga yau banda matsala da hakan. Ko takan Mansoor banbi ba nai ficewata gaba ɗaya daga gidan. Napep na tare zuwa garejin su Yaya Musaddiq. Na samu suna shirin shiga sallar azhar, sai dai shi Yaya bai kai ga tafiya ba yana ƙoƙarin ɗaura alwala ne. Tun kafin na ƙarasa inda yake na fahimci ya zuba min ido.        “Lafiya kike?”.    Ya faɗa dai-dai ina isowa gabansa shi kuma yana wanke ƙafarsa. Mai makon amsa sai na tura masa baki. Kansa ya girgiza kawai yana sake faɗin, “Je can ki zauna muyi salla to, idan na dawo sai kiyi taɓarar”. Daga haka ya wuce ya barni a wajen dan ya kammala alwalar...   💫´⊙ω⊙💫⊙ω⊙💫⊙ω⊙`💫                      Zaune yake a falo tare da Hayatu da Juliet, tab.. ce a hannunsa, ƙafafunsa miƙe saman Centre table da aka turo gabansa sosai. Hankalinsa gaba ɗaya nakan screen ɗin tab ɗin, hannunsa ɗaya rike da haɗaɗɗiyar chocolate yana ci a hankali tamkar baya so. Yayinda Juliet ke bayani akan abinda ya zaunar da su ɗin, dan itama dai laptop ce a hannunta, sai Hayatu dake riƙe da takardu ta gefenta. Abinda juliet ɗin ta faɗa na ƙarshe ne ya sakashi ɗagowa cikin rashin sakewar nan tasa ya zuba mata ido. Da sauri ta risinar da nata dan Maash nada wani kwarjini dakan hana mai kallonsa iya masa kallon ido cikin ido na tsawon lokaci, koda kayi jarumtar yin hakan da zaran shi ya zuba nasa cikin naka zaka ji ka takura. A ɗan daƙile ya ce, “Ina son magana da Mustapha. Sannan ai cancel ɗin Thailand a cikin schedule namu a maida Finland”.        Atare su duka biyun suka amsa masa dan zancensa ya shafi kowannensu. Babu ɓata lokaci kowanne ya shiga yin abinda aka saka shi. Juliet ce ta fara ɗagowa cikin harshen turanci tana tambayarsa, “Sir komai zai zama ne de same date?”.             Kamar baima jita ba aikinsa yake, sai da ya mula dan kansa sannan ya bata amsa da “Uhm”. Cikin girmamawa ta jinjina kanta da amsa masa ta cigaba da aikinta. Dai-dai nan shima Hayatu ya taso daga inda yake da waya a hannunsa. Ta gefensa ya ɗan tsaya cikin risinawa ya miƙa masa. Batare daya ɗago ba a hankali ya furta, “Sa a hans free”. Da sauri Hayatu ya maidata hans free, sai ga muryar wancan da ya kira da Mustapha rangaɗam. Duk da a cikin waya yake cikin girmamawa ya gaishesa, zaka tabbatar da hakanne ta yanda yake magana cikin ƙanƙan da kai. Shikam kamar yanda ya saba ya amsa a taƙaice. Sannan suka tsunduma maganarsu, duk dai akan harkar business ne, mafi yawan maganar kuma Mustaphan keyinta.. ba wata doguwar magana sukai ba ya barsa suka cigaba da magana da Hayatu. Dai-dai Hayatun na ajiye wayar shima alamar sunyi sallama ɗaya daga cikin securitys ɗin gate yay sallama tare da yin knocking. Hayatu ne yaje garesa yana amsa masa sallamar. Jin abinda security ɗin yace ya sashi ɗan wara ido waje. Sai kuma ya juya cikin falon da sauri. Cikin ɗan yanayin rawar harshen wanda ya shiga ruɗani ya ce, “Sir Baba prof.. ne a gate”.       Cak Maash ya dakata da abinda yake, sai kuma ya lumshe idanunsa tare da buɗesu luuu gaba ɗaya akan Hayatun. Bashi da alamar cewa wani abu, Hayatu kam duk ya ƙagu yace ɗin. Idanun nasa ya maida ga tab ɗin abinsa batare da yace komai ba. Sake birkicewa Hayatu yayi, sai dai baida tacewa.         “A buɗe masa”.      Zabura Hayatu yay yana sauke nannauyar ajiyar zuciyar da sai da ta saka Juliet danne dariya. Dan haka ya harareta ya nufi hanyar fita da sauri. Shiko Maash aikin gabansa ya cigaba dayi hankali kwance. Mintina huɗu ba'a cikaba sai gasu kuwa. Baba prof.. ne a gaba. Tun a taku biyu ya tsaya yana bin falon da kallo, kafin ya sauke ƙyawawan idanunsa na tsufa akan santalelen jikan nashi mai ji da lokacisa. Murmushi ya saki a hankali, sai kuma ya cigaba da shigowa cikin falon guards ɗinsa guda biyu biye da shi. Sai Hayatu a gefe. Juliet ma tuni ta miƙe tsaye. Cikin girmamawa ta shiga gaishesa, ya amsa mata da kulawa, har lokacin kuma Maash bai motsa ba balle ya kalla kakan nasa. Hayatu ne yayma guards ɗin Baba prof... da Juliet magana dan haka suka fice suka barsu su biyu.          A karo na babu adadi Baba prof.. ya sake sakin murmushi. Idanunsa akan Maash ya ce, “Fushinne har yanzu? Common sweetheart ya kamata ka huce mana. Kaifa yanzu babban mutum ne ba little Awwab ɗin nan ba mai hawa saman wuyan grandpa ɗinsa yay doki saboda fitinarsa. Be a man mana my baby boy”.       Fuska Maash ya sake tsukewa. Batare da yayi magana ba ya dangwarar da tab.. ɗin hannunsa yana miƙewa kamar a fusace zai wuce. Caraf Baba prof.. ya damƙo hannunsa, jawosa yay kawai ya faɗa jikinsa ya rungumesa tsam-tsam yana dariya. Sun jima a haka Maash nata faman sauke ajiyar zuciya, yayinda Baba prof.. keta murmushinsa shi dai. Sai da ya tabbatar ya gama haɗiyar zuciyar kafin ya ɗagosa. Hannu yasa saman kansa ya birkita gyararriyar sumarsa da yau bai ɗaure ba. Babu shiri Maash ya saki murmushi daya sake ƙawata ƙyawunsa. Baba prof.. kuma ya ƙyalƙyale da dariya tare da jamasa dogon hancinsa sannan ya sake maida hannunsa kan sumar tasa ya shiga kwantar da ita yanda take.        “Dibeka so cute idan kana murmushi. Amma ka dinga ɗaurema mutane fuska har ni ɗin ma Kakanka ban tsira ba. Kai nidai naga takaina da kai balaraben Nigeria”.       Murmushin Maash ya sake yi, batare da yace komai ba ya girgiza kansa kawai yana nufar kujera ya zauna kamar yanda Baba prof.. yayi. Cikin girmamawa ya gaida kakan nasa, shiko ya amsa masa cike da kulawa, sai kuma yabi falon da kallo yana cigaba da faɗin, “Mutumina alƙawarin ALLAH dai ya cika ka dawo mafari. Hakan nada ƙyau kuma naji daɗi kwarai da gaske. Ina fata kuma za'amin afuwa da rashin cika alkawarin dawowa da nai jiya. Gangar jikin nawane kawai acan, amma zuciyar na nan. Shiyyasa ma ina sauka a Lagos ko gida banje ba na sake biyo jirgi zuwa nan ɗin.”          “Ba komai ya wuce ai, ina fatan ka dawo cikin ƙoshin lafiya”. Maash ya faɗa cikin tausasa harshe duk da dai maganar da ƙyar take fita. Baba prof.. bai damu ba, dan yafi kowa sanin wanene jikan nasa. Wannan yanayin nashi kuwa halittarsa ce, tun yana ƙaraminsa baida sakewa da mutane. Sannan haka yake dai babu yawan magana. Wasu abubuwa da suka faffaru kuma suka sake maidashi dunɗun dukum ya zama miskilin gasken gaske. Gashi nan dai babu yabo babu fallasa a ɓangaren kirki. Dan babu wanda ke ɗaga masa yatsa bai karya ba. Ya iya rikici da rigima ƴar gaske. Dan tabbas Maash akwai rikici, tsagerane na bugawa a jarida, sai dai yanayinsa na shiru-shiru yasa sai ya zuba maka tsiya yay kamar bashine yayi ba, in kuma za'a tambayi mutum dubu su shedesa suma akan bashi ɗin ne yay ba. Sai dai su da sukai masa sanin ciki da bai na rayuwa, musamman ma shi kakansa da mahaifinsa da mahaifiyarsa sun san shine ya yin......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 - 𝒕𝒘𝒐_ .......“Da kika gudo kika barni yanzu ban kawo kaina ba?”. Mansoor ya faɗa dai-dai suna ƙarasowa inda nake shi da Yaya Musaddiq. Baki na ɗan murguɗa ta cikin mask ɗina, a zahiri kam nai ƙasa da kaina sai dai bance komai ba. Sai Yaya Musaddiq ne ke dariya. Ni dai bance komai ba, sai da Mansoor ya sake faɗin, “Bazaki ban haƙuri ba?”.        Bakin na sake turawa. Sannan na ce, “To kayi haƙuri”.      Murmushi Mansoor yay yana kaiwa zaune. “Ai dole ma na haƙura dan bana iya dogon fushi da ke. Ga yaya Musaddiq nan ma shaida ne”.      Murmushi Yaya Musaddiq ya sake saki, ni kuma na ɗan harari Mansoor ɗin. Shima murmushin yay a lokacin, tare da ɗan taɓe bakinsa ya ɗauke kansa gefe. Sai kuma ya sake juyowa gareni. “Mi MD yace dake?”. Mask ɗin na cire ina kumbura fuska kamar MD ɗinne har yanzu a gabana. Labarin komai na basu, shi kuma ya faɗama Yaya Musaddiq komai tun daga farko. Sosai naga farin cikin abinda nai ɗin a fuskar Yaya Musaddiq, har takai ya kasa haƙuri ya dafa kaina da faɗin, “ALLAH yay miki albarka Kandalata. Abinda kikayi shine dai-dai, dan nima anan banga wani dalilin da za'a baki ƙyauta harta mota ba ki amsa. Ki cigaba da haka, dan gaskiya itace RUHIN dukan MUSULMI na ƙwarai. Sannan ita mace tana bine ta kowacce hanya domin kare mutuncinta da kimarta a al'adance da kuma addinance.”          “Nagode Yaya”.     Na faɗa cikin zumuɗi da jin daɗi. Dan kalamansa sun ƙaramin ƙwarin gwiwa ƙwarai da gaske. Ganin Mansoor bai tanka ba na ɗan juyo na kallesa. Murmushi ya sakar min, nima sai na mayar masa da murtani. Kaina tsaye na ce, “Amma kaima zaka maida musu?”.         “In sha ALLAHU”.    Ya bani amsa cikin tabbatarwa. Nan ma nayi farin ciki, daga haka na mance da dukkan damuwata muka koma hira mai daɗi. Harga ALLAH ina matuƙar son waɗan nan mazajen biyu, dan sunada matuƙar muhimmanci a rayuwata. Sun kuma taka rawa mai ƙarfin gaske da in har zan nuna kaina sai na haɗa da koda inuwarsu ce. Ko kaɗan bamuyi maganar videon nan a wajen ba saboda tsaro, sai da muka koma motar Mansoor sannan muka ƙarasa. Yaya ya bada shawarar mu binciki ɗan sanda mai gaskiya da zamu iya damƙama video ɗin kawai batare da sunanmu ba, kokuma mu haƙura a gogeshi mubar zancen, ko bajima ko ba daɗe idan har halin mutumin nan ne hakkin rai bazai barsa ba. Amma maganar yin fito-na-fito da shi bama ta taso ba a garemu. Harga ALLAH maganar Yaya Musaddiq bata mun daɗi ba, taya kawai dan mutum nada kuɗi a dinga nuna tsoronsa haka bayan akwai hujja mai ƙarfi a tare da mu. Amma sai na danne yanayina nace mu sakesa a media kawai, dan a wannan zamanin banga wani ɗan sandan da suke hasashen samu ba. Su duka basu goya da bayana ba. Shima Mansoor yana bayan shawarar Yaya Musaddiq ɗin ne. Dole nima nabi ra'ayinsu, duk da tun farko dama ni na fara kawo shawarar kaiwa ƴan sandan, banbancin shawarar tasu da tawa ƙalilance. Bayan mun kammala tattaunawar munbar Yaya anan ni kuma Mansoor ya wuce kaini gida. Muna tafiya muna hirarmu mai daɗi, duk da yaso mu tsaya muci abinci naƙi yarda da hakan. Koda mukaje gidan ma sai da muka ɗan ƙara taɓa hira, duk da dai hirar tamu ma dai akan bikinmu ne, dan iyayensa zasu sake zuwa a satin sama domin saka rana. Ya kuma tabbatar min da bawani lokaci mai tsayi za'a saka ba. Dan shi ya gama kammala komai amarya kawai yake jira. Naji kunyar furucin nashi sosai, dan haka na ɓalle murfin motar na fita abina. Ina jiyo sautin dariyarsa ban kulashi ba, sai da zan shige gida gaba ɗaya ne na juyo. Ido ɗaya ya kashe min, aiko nai wuff na afka ciki..          A falo na samu duka mutanen gidan tsaye carko-carko har Abbas yau yana gida. Ga kayana a barbaje an musu filla-filla. “Yauwa ga ɓarau-ɓarau ɗin nan ta dawo”. Furucin Bibaa ya dawo da hankalina kansu. Kafin nai wata magana kawai naji saukar mari. Duk da azabarsa ta matuƙar ratsani banyi ko gezau ba. Sai wanda ya marenin na zubama ido kawai, ba kuma kowa bane face Abbas. Nunani yay da ɗan yatsa tamkar zai tsokale min ido ya ce, “K dan uwarki kawo sarƙar Mom da kika sata, shegiya ɓarauniya mai kama da aljanun daren salla”.         Cikin dakiya irin tawa na ce, “Karka sake zagar min uwa. Sata kuma kanku ya kamata ku bincika, tunda kune ke shiga ɗakin Mom ɗin ai. Ni ba ɓarauniya bace, kuma in sha ALLAHU babu wani tsananin rayuwa da zaisa na aikata ta”.      Daga haka na duƙa domin tattare kayana. Amma sai ji nai an shaƙoni ta baya. Har hijjab ɗina na matsemin maƙoshi. Da sauri nasa hannu naja hijjab ɗin sama. Sannan na miƙe. Baby ce mai riƙon nawa yanzu, itama hannu ta ɗaga zata maran, sai dai kafin ta sauke min ni na sauke mata nawa yatsun biyar akan farar fuskarta. Saurin janye nata hannun tai tare da sakina ta haɗa duka hannuwanta biyu ta riƙe kuncinta. “Karki soma fara wannan wasar dani a gidan nan, shima daya maran ɗin ba ƙyalesa nai ba balle ke shashasha”.        “Toni bari na marekin sai ki haɗa ki rama” Mom ta faɗa tana wani zaburowa kaina. Banyi ko motsi ba harta ƙaraso ta maran ɗin a haggu da dama. Sannan ta shaƙoni. Kakari na fara, amma ko gezau bata da alamar sakina. Sai ma faɗi take, “Dan ubanki ina sarƙata? Ina kikaje kika saida ta? Dan nasan fitar da kukai ke da annamimin mai saki yin komai a gidan nan abinda kuka je saidawa kenan. Kuma wlhy bazan yarda ba, sarƙata ko kuɗinta”.      Zuwa yanzu kwata-kwata bana iya numfashi da ƙyau, hakan yasa Abba da tun ɗazun baice komai ba ya ƙaraso da sassarfa yana ƙoƙarin cire hannun Mom ɗin daga wuyana. “Kinga Jalilah saketa Please. Sakarta ta faɗa inda take kada ki kasheta mana”. Sam bata da alamar sakin nawa kuwa. Dan haka ya tureta da ƙarfinsa har sai da tai taga-taga zata faɗi, ni ma dai zubewa nai a wajen ina sauke wahalallen numfashi a gwagwgwame. Ga tari dake neman sarƙeni. Da sauri auta yazo gabana ya duƙa yana miƙamin ruwa. Banyi musu ba na amsa, dan ina buƙatarsa. Sauri-sauri na fara sha, sai ji nai an kaɓe ruwan ya zube jikina gaba ɗaya. Yayinda Auta ya fasa wani kukan azaba. Da sauri na tashi zaune, dan bata ruwan da aka zubarmin nake ba ta shi nake. Yaron na sona sosai a gidan, kawai dai dan baida yawan magana ne sai idan shi yaso, dan miskili ne na bugawa a jarida. Ba komai akai masa ba, Baby ce data figesa daga kusa dani kawai yake ma ihun kuka, Bibaa kuma na huci alamar itace ta kaɓar da ruwan da ya bani......   ✨(☯෴☯)(☯☯)(☯෴☯)✨           Badan Maash yaso ba dole ya shirya suka fita da Baba prof.. zuwa Company, daga can suka tsaya sukaci abinci a wani haɗaɗɗen restaurant. Daga haka suka wuce airport domin masa rakkiya, dan ya rasa jirgin sha biyu sai ya sake bucking na yamma. A hanyarsu ta zuwa airport ɗin ne Baba prof.. ke tsegunta masa yama yarinyar da tai hira da shi ɗazun ƙyauta amma ta dawo masa da shi. Dan haka mamakin yarinyar ya kasa barinsa har yanzun.      Shiru Maash dake saurarensa yay tamkar bai ji ba. Sai dai a ransa faɗin yake (Ai bazata amsa ba. Ita dake harin miliyan ɗari biyar). “Wai baka jini bane?” Baba prof.. ya katse masa tunani. Cikin basarwar tasa da magana ciki-ciki ya ce, “Ban san mi zance bane Grandpa”.     “A komai ai dama kai baka da abin cewa. Ko akan hirar ya kamata ma ka tambayi dalilina nayin hakan, amma ka share abinka. Awwab wai yaushe ne zaka canja? Anya matar da zaka aura zata iya ɗaukar wannan baƙin halin naka kuwa?”.        “Ni nace zanyi aure ne?”.    Ya faɗa a wani yanayi mai kama da jin zafi. Murmushi kawai Baba prof.. yay yana girgiza kansa. Sai kuma ya ce, “Oh haka zakaita zama kenan?”.     Bai tanka masa ba sai ma ɗauke kansa da yay. Shima Baba prof.. ɗin sai bai sake magana ba har suka iso. Sama-sama sukai sallama, batare da yaga tafiyarsu ba ma yace Tijjani ya juya da shi gida.        Abinka da lafiyayyar mota, cikin ƙanƙanin lokaci suka iso gidan. Security ya buɗe musu gate cike da girmamawa. Tun kafin motar ta tsaya idanunsa suka sauka akan matashin saurayi da ke zaune a ɗan tudun da akai wajen flowers, Hayatu na daga gefensa zaune a kujerar roba dan bada shi suka fita ba. Sai dai tunda motar ta shigo ya miƙe tsaye. Suna gama dai-daita parking kuma ya iso da sauri kafin ma Guards dake tare da su ko Tijjanin ya fito ya buɗe masa shi ya buɗe masa.       “Sannunku da dawowa Sir”.   Hayatu ya faɗa yana rissinar da kai. Shima kan kawai ya jinjina masa yana kamo gefe da gefen jacket ɗinsa ya saka maɓallinta guda ɗaya jal dake a tsakkiya. Batare da ya sake kallon inda saurayin nan da yay galala yana kallonsa ba ya wuce hanyar falonsa cikin takun dake tabbatar da shi a sadaukinsa, kai daka gansa kaga tsayayyen namiji da iskar lokaci ke kaɗa masa. Wayoyinsa biyu da ya fita da su Hayatu ya kwaso a motar, sai wata ƴar ƙaramar bag mai ƙyau da Baba prof.. ya bashi, ba komai bane a ciki kuma sai turare mai azabar tsadar tsiya da ƙamshi. Saurayin nan ya kalla ya ce, “Ka jirani anan Sani ina zuwa”.        Cikin girmamawa saurayin ya amsa masa da “To Yaya a fito lafiya”. Zaune ya samesa bayansa jingine da kujera ya lumshe idanu alamar gajiya. A hankali ya ajiye masa wayoyin gefensa, bag ɗin kuma a saman Centre table. Sai kuma ya nufi freight ya ɗakko ruwa da glass cup. A gabansa ya zo ya ajiye, tare da tsiyayawa ya miƙa masa cike da girmamawa. “Sir ga ruwa”. Shiru kamar bazai motsa ba, sai kuma ya miƙa hannu ya amsa batare da ya ɗago ko ya buɗe idanu ba. Ɗan jimm Hayatu yayi, sai kuma ya sake daurewa ya ce, “Sir dama yaron da zai yi aikin nan ne yazo gashi can a compound, a shigo da shi ne ka gansa?”.          Nan ma yaja wasu sakanni kafin yace, “Shigo da shi”. Da ga haka ya ɗan ɗago ya kurɓi ruwan, sai kuma ya sake maida hannunsa a goshinsa yana ɗan murzawa........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_ ......A tare Hayatu da saurayin sukai sallama. A saman lips ya amsa musu. Suna ƙarasowa saurayin ya zube a ƙasan lallausan carpet ɗin tsakkiyar kujerun, sai faman kalle-kalle yake kamar wanda ya buɗe ido da ga makanta. Sai da Hayatu ya ɗan zunguresa da ƙafa sannan ya dawo hayyacinsa ya ɗan nutsu. Ganin idon Maash a kansa ya sake nutsuwa tare da faɗin, “Ranka ya daɗe ina wuni”.          A hankali Maash ya ce, “Lafiya, miye sunan ka?”.      “Sani”. Ya bada amsa da sauri. “Kayi karatu?”.    “Eh ranka ya daɗe, har matakin N.C.E na kai. Sannan na sauke Alkur'ani tare da littatafan addini masu yawa”.          Kai kawai Maash ya jinjina masa, dan shi hausan ma ba wai duka yake ganewa ba. Sai dai yaji dukkan bayanin saurayin. Hayatu ya kalla, dan haka yay saurin gyara tsaiwarsa da ɗan matsowa kusa da shi. Dan shi koda ido Maash ya kallesa yasan mi hakan ke nufi. Kai tsaye ya ce, “Na sanshi sosai Sir farin sani, dan ɗan uwana ne, da mahaifiyarsa da mahaifina uwarsu ɗaya ubansu ɗaya. Sai dai su anan Kano suke. Yasan ciki dabai na garin Kano, sannan ita kanta yarinyar ma ya santa a dalilin shirin da take gabatarwa na matasa, har hira ta taɓa yi dasu wata biyu da suka shige lokacin bai kammala makarantarsa ba”.            Nanma shirun yay ƙafarsa ɗaya akan ɗaya yana kallon saurayin kawai, sai da ya mula dan kansa sannan ya furta, “Ka tabbatar zai iya?”.        “In sha ALLAHU zai iya Sir. Kuma zai riƙe sirrin dan in ma ya tona kamar kansa ya tonama asiri ne. Mu bamu sanshi ba bamu da alaƙa da shi idan aka samu kuskure”.       “Fine.”   Ya faɗa a taƙaice yana miƙewa abinsa. Ƙofar bedroom ɗinsa ya nufa, sai da yana gab da shiga corridor ɗin ya ce, “Ka bashi key ɗin mota da 500k na mai. Sallamarsa sai ya gama aiki”. Daga haka yay shigewarsa. Waro idanu sosai Sani yayi, jikinsa na rawa ya ce, “Yaya dubu ɗari biyar fa. For mai ɗin mota kawai? Na shiga uku ni Sani ɗan inna”.         Dariya abin ya bama Hayatu, sai dai baiyi ba yay murmushi kawai da faɗin, “Kaga tashi muje waje sai kai murnar. Ka jirani bara na kai masa wannan”.      Ai kafin ma Hayatu ya rufe baki Sani ya kai ƙofa da sassarfa...        _😂Sani a taimakan dana data mana🤣😝._           💢💦💢💦💢💦💢 A rikice Yaya Musaddiq ya iso gida sakamakon kiran da nai masa ina kuka. Sai dai kafin ma nakai ƙarshen abinda zan gaya masa Baby ta kaɗar da wayar tawa gefe ta daki tayis. A take tai ƙarar fashewa. Koda na ɗagota screen ɗin yay rugu-rugu ta koma fari gaba ɗaya alamar ta samu matsala. To anan ne fa na kasa haƙuri, bamma san sanda nai kukan kura a kanta ba sai ganina sukai na haye ruwan cikinta ina jibga tamkar ALLAH ya aiko ni. Aiko Bibaa da Abbas suka shigar mata suma suka hau dukana. Auta kuwa ya hau ihu da kururuwar kuka. Abba zai rabamu Mom ta riƙesa da makircinta. Sarkin yawa yafi sarƙin ƙarfi, duk da nima na more akan Baby suma sun dakeni sosai harda jimin ciwo. Wannan faɗa bai rabu ba sai da Yaya Musaddiq ya shigo. A haukace ya faɗo falon batare da neman izini ba ya hankaɗe Abbas gefe tare da Bibaa. Sannan nima ya ɗagani akan Baby. Sake yo kaina Abbas yay Yaya ya shiga tsakkiyar mu yana daka masa tsawa. “Abbas!! Kai miyasa baka da wayo ne? Maimakon ka rabasu matsayinka na babba amma rashin hankali da kai ma akeyi?”.         Maimakon Abbas ya bada amsa sai Mom ce ta taso a fusace taba Yaya Musaddiq ɗin amsar. Daga ni har shi take haɗawa tana zagewa da kirani ɓarauniya, kai har iyayenmu ma haɗowa take. Yayinda ƴaƴanta ke faman huci kamar zasu daki Yayan shima. Duk da abinda ake Abba na falon ya gagara sake cewa komai.     Karon farko dana ga ɓacin ran Yaya a fili game da abinda ake mana a gidan. Dan muryarsa har zuga take wajen faɗin, “Mom ki daina danganta Samraah da sata dan bata taɓa yima wani aka gani ba. Fitarta ta yau kuwa kowa yasan inda taje tunda abune a bayyane. Ya kamata dai ki binciki sarƙarki a tsakanin ku da kuke gidan zaune.” daga haka yaja hannuna dan mu fice. Amma sai Mom ɗin da Abbas suka sha gabanmu. Abbas ne ke faɗin, “Kai har ka isa ka fiddata anan bata ajiye sarƙa ko kuɗin sarƙa ba. An kuma kirata ɓarauniyar ko akwai abinda zakayi ne?”.         Wani daƙilallen murmushi yaya Musaddiq ɗin ya saki a karo na farko. Sai dai baice komai ba ya sake jan hannuna zamu raɓasu mu wuce.    “Mussadiq!”. Abba ya ambata a karo na farko. Cak ya dakata, sai dai bai juyoba bai kuma yi magana ba har sai da Abban ya sake magana. Still dai hannun nawa na riƙe a nashi muka dawo gaban Abban. Da hannu yay masa nuni daya zauna. Nan ɗin ma kamar bazai zaunaba ɗin sai kuma dai ya zauna. Hakan yasa nima na zauna a kusa da shi. Mom ya kalla ita da su Abbas suma yace suzo su zauna... Kusan mintina uku falon yay tsit sai ƙwafa da Mom keyi a jajjere tana harararmu ni da Yaya Musaddiq. Sai da Abba ya tabbatar kowa zuciyarsa ta nutsu kafin ya fara magana. “Bana jin daɗin wannan rayuwar da akeyi a gidan nan sam. Mu ace kullum sai maƙwafta sun jiyomu muna ihu da hayaniya kamar wasu marasa abinyi ko wanda basu je ajin makaranta ba. Bakwa ganin hakan zubarma da kammu mutunci ne?....”       “Abban Abbas kaje ga maganarka kai tsaye nifa bana son wani kwana-kwana. Batun sarƙata ake anan ba wani mutunci ko yanda maƙwafta ke kallonmu ba. Su ya dama, sun kuma ga zasu iya ne. Dan haka ka musu magana su futomin da sarƙata in har ana son zaman lafiya a gidan nan. Inba haka ba wlhy police station zan kai su. Ai acan dole su fito da ita ya arziƙi ko tsiya.”     Daga haka ta miƙe fuuu tabar falon. Shima Abbas miƙewarsa yay ya fice. Baby ta taɓe baki itama ta miƙe ta fita. Bibaa dai bata tashi ba, amma itama sai harare-harare take. Gaba ɗaya yanayin Abba ya sake sauyawa, sai dai mun san babu abinda zai iya. Ilai kuwa hankalinsa ya maido kammu. Babu kunya babu tsoron ALLAH ya shiga faɗin, “Ke Samraah ki fito musu da sarƙarsu ko ki faɗi ina kika saida aje a amso kinji, wlhy wannan fitinar ta isheni. Ku barni da abinda ya daman mana”.           Kai Yaya Musaddiq ya girgiza kawai, yayinda ni kuma nakema Abban wani kallon takaici da baƙin ciki. Zanyi magana Yaya Musaddiq ya dakatar dani da faɗin, “Amma Abba bai kamata dan an nema wani abu an rasa ace Samraah ce ta ɗauka ba tunda ba ita kaɗai bace a gidan. Sannan ba kuma taɓa kamata akai da halin ba balle a kafa hujja da ita ɗin ce ba. Idan Samraah ta ɗauka sarƙa mizatai da shi. Karfa a manta tana aikinta, sannan ma kowa shaidane Mom bata taɓa barin tsakanin ni ko Samraah da Hafizzullah mu shigar mata ɗaki tun muna ƙanana. Amma tunda har kaima ka yarda da ita ɗince ta ɗauka ita Mom ɗin ta faɗin kuɗin sarƙar tata in sha ALLAHU za'a biyata. Amma kuma da ga yau zamu cigaba da gayama ALLAH kuma zamusa a tayamu kafin wani a cikinmu yabar duniya ALLAH ya tona asirin wanda ya ɗauki sarƙar”.         “Amin ya rabbi, ba addu'a a Nigeria ba ku tafi gaban ka'aba kuyi mara mutunci. Ai dama na daɗe da sanin kaima ƙwallen shege ne nata ne kawai ya fita ita fitsararriyar. Sarƙata kuma naira dubu ɗari huɗu na sayeta sai a biyan kuma bana son ya wuce yau ɗin nan. In ba hakaba wlhy kaiwa police station babu fashi”.      Murmushi kawai Yaya yayi, batare da yace komai ba ya miƙe. Kallona yay ya ce, “Tashi ki tattara kayanki ki maida ɗaki zanje na dawo”. Daga haka ya fice ni kuma na miƙe na shiga tattara kayan. Baka jin komai a gidan sai banbami da masifar Mom da zagin da take loda mana. Amma Abba kamar an ajiye gunki domin ado ko uhum bai sake cewa ba. Ni dai na tattare komai na nufi ɗaki, dan tuni na daina hawaye sai zuciyata dake wani irin suya da ƙuna tare da sake jin tsanar gidan da kowama na cikinsa. Yanda zuciyata ke mun zafi da raɗaɗi ji nake kamar nai kiran Mansoor nace masa gobe iyayensa suzo a tsaida bikinmu sati ɗaya kawai. Ni ko babu wani biki a ɗaura auren kawai na tare. Amma dai na dake dan bazan iya hakan ba, hasalima ni ban taɓa nunama Mansoor munada wata matsala a gidanmu ba, saboda hakan sirrinane bakuma zan iya tona sirrin cikina ga saurayi ba watarana yay min gori da hakan ko ya dinga kallon ƴan uwana a wulaƙance koda munyi aure. Koma dai mi suke mana su ɗin jininmu ne dai bamu da wanda ya fisu. Shiko wataran zai iya canjawa koma ya ɓata ɓat a rayuwata duk da bana fatan hakan kodan tsananin ƙauna da soyayyarsa da nake ji a cikin zuciya da ruhi na.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒇𝒐𝒖𝒓_ ......Sallamar Yaya Musaddiq da naji a falo bayan sallar isha'i ta sani miƙewa daga kwancen da nake zazzaɓi ya rufe ni. Nasan kuma ba komai ya jamin hakan ba sai caskalen da mukayi dan da gaske naci duka a wajensu. Daga inda nake na zubama Yaya Musaddiq daya dire baƙar leda a gaban Abba idanu na dake cika da ƙwalla. Yayinda kunnena ke sauraren abinda yake faɗa.        “Abba ga kuɗin sarƙar nan a bata. Naira dubu ɗari huɗu ne kamar yanda ta faɗa”. Daga haka ya miƙe ya nufi hanyar fita. Cikin sauri na take masa baya batare da nabi takan shewar da Mom keyi ba kuɗin daya ajiye ɗin a hannunta dan bata bar Abba ko taɓawa yayi ba. “Yaya!”. Na kirasa da sauri ganin bai san ina bin bayansa ba. Tsayawa yay tare da juyowa yana kallona. Ina isa garesa na kamo hannunsa na wani ƙankame ina mai fashewa da kuka mai ƙarfi. Shiru kawai yay yana kallona. Tsahon minti ɗaya batare daya ce komai ba ya kama hannuna kawai muka nufi ɗakinsa. A bakin tabarmarsa ya zaunar dani, sai kuma ya sake fita batare da yace dani komai ba nan ma. Tun ina kuka daga zaune har na zame na kwanta Yaya bai dawo ba. Sai da ya ci kusan mintuna goma sha biyar sai gashi da ledar magani da dafaffiyar indomie. Zuwa sannan nabar kukan sai jan ajiyar zuciya nake kawai.      Abincin ya tasani gaba mukaci tare cikin lallashi, ya kuma bani magungunan nasha suma da ƙyar dan bana son magani, allura kam tsoron da nake mata ai ba'a magana. Ganin baida niyyar cemin komai har sannan akan kuɗin daya basun muryata na rawa nace, “Yaya ina ka samu kuɗi ka basu bayan kasan kuma ban aikata ba. sharrinsu ne kawai ya tashi ko kuma makircin Mom dan ta samu kuɗin dama”.      Ɗan murmushi ya saki tare da ɗora hannunsa a kaina. “Ki kwantar da hankalinki kada kuma ki damu da abinda sukayin, tunda ALLAH yasan bake kika ɗaukar musu kaya ba ya rage nasu. Bana son naga kina wannan kukan sam. Kuɗi kuma wanda nake asusune dama akan hidimar aurenki tuni, ALLAH zai kawo mana mafita kafin lokacin dan shi mai rahama ne mai jin ƙai, dan ko a yanzu da suka amshi wannan nasan bazamu kunyata ba daga abinda ta rage mana. Kar kuma ki saka abinda sukayi ɗin a cikin ranki ko kice sai kin rama dan na sanki kuma bajin magana kike ba, ki bari UBANGIJI da kansa ne zai rama miki wannan faɗan, dan bazan gushe ba ina mai kai masa ƙarar su garesa, kasancewar sa Sarkin daya haramta zalunci a karan kansa balle ga bayinsa nasan bazai barsu ba Samraah. Ki cigaba da haƙuri kinji, watarana sai labari, komai zai shuɗe tamkar ba'a taɓayi ba. Kwana nawa ma ya rage miki a cikin gidan, ƙarƙari ki ƙara wata biyu fa, dan ko yau mun sake magana da Mansoor a weekend ɗin nan iyayensa zasu sake dawowa a tsaida rana, dan su sun ma so ayi komai a randa sukazo Abba ne bai basu haɗin kai ba. Ke dai kawai ki cigaba da haƙuri, dama in aski yazo gaban goshi yafi zafi”.        Wasu hawayen ne masu zafi suka sake ɓalle min, Yaya Musaddiq yasa hannu yana sharemun da murmushinsa. Wanda ni nasan yana yinsa ne kawai amma shima ransa a ɓace yake matuƙa. Dan idanunsa jazur suke sosai.....     💦💦💦💦💦💦         Da ƙyar Sani ya iya nutsuwa Hayatu ya masa bayani dan shigar 500k ɗin nan a account ɗinsa ta rikitashi matuƙa, daɗin daɗawa kuma Hayatu ya ƙara masa da 100k ƙyauta injisa kash a hannu. Ga kuma key ɗin mota da zai yi aikin da ita. Sai kawai Sani ya fashe da kuka. Dan abunne yazo masa ɓakatatan babu zato. Harga ALLAH zai iya rantsuwa bai taɓa ganin dubu ɗari biyar a dunƙule ba. Dan su talakawane sosai, ko karatun nan yayisane da ƙyar cikin buga-buga saboda yana matuƙar son yin karatu a rayuwarsa. A hakanma da ƙyar aka kammala, dan dai ALLAH ya bashi ilimine ma dan yanada basira sosai.. Kasancewar Hayatu har gida yaje yayma babansa bayani akan ogansa ya ɗauki Sanin aikin tuƙi koda yaje gida da mota babu wanda ya tambayesa, sai ma murna da suka taya shi. Kuɗi kuwa ko na wajen hayatu ma bank ya wuce aka saka masa su. Da dubu ashirin kawai ya shiga gidansu kamar yanda Hayatu ya bashi shawara, gaba ɗaya a yinin wannan ranar bakinsa yaƙi rufuwa. Motar ya kai aka duba kamar yanda Hayatu ya umarcesa, bayan an tabbatar komai zam ya koma da ita gida...         🌟💞🌟💞 🌟💞 🌟       A ɓangaren su Hayatu da ogansu Maash kuwa babu wanda ya sake saka shi a ido sai da la'asar, dan shi baya sakaci da ibadarsa, duk wanda ya san Maash ya sanshi akan hakan. Mutum ne mai matuƙar riƙo da ibada, ko'a tsakkiyar taron turawa yake, komai muhimmancin kasuwancin da yake in har lokacin salla yayi sai yay excusing kansa ya fita yayita, koda kuwa zai iya rasa wannan kasuwancin ne hakan bai damesa ba. Koda ya dawo sallar ma ciki ya koma abinsa. Sai bayan sun dawo sallar isha'i ne Hayatu ke sanar masa saƙon da gidan tv'n ALHERI suka turo game da amsa gayyatarsu da yayi. Sun buƙaci ya bada lokacin da duk yake so daga takwas na safiyar gobe idan ALLAH ya kaimu har zuwa tara na dare.       Sai da yay ɗan jimma kamar bazai tanka ba kafin ya kalla agogonsa. Da wani salon lumshe idanu dai-dai yana ɗagowa ya furta, “Ƙarfe nawa Abubakar zai zo?”.      “Eh Sir kamar yace zuwa four na pm ne. Dan zai baro Abuja kamar Three”.     “Kafin lokacin akwai wani abu ne?”.      “A'a gaskiya. Dama dai ganawa da Senetor Kibiya ne, kuma kace Juliet tai magana da shi.”            “Okay ka sa musu ten to eleven kawai. Dan awa ɗaya zan iya basu”.      “Ai hakama sun gode Sir”.    Hayatu ya faɗa yana danne mamakinsa. Da ga haka Maash bai sake tankawa ba. Dan haka Hayatu ya fice ya barsa dan ya huta..... (◕‿◕)➜(。◕‿◕。)➜(◕‿◕)          Washe gari Monday da ƙyar na iya danne zuciyata nai aikin gidan kafin nai shirin fita. Nayi aikinne kawai dan nasihar Yaya Musaddiq. Ina kammalawa kuma ko karyawa ban ba nai ficewata. Na samu shima Yaya Musaddiq ya shirya, dama yace min yanada uziri akwai aikin wani mutumi da zai ƙarasa saboda yau da safe zai zo ya amsa motarsa. Tunda muka fara tafiya babu wanda ya tankama ɗan uwansa tun bayan gaishesa da nayi, a haka har muka iso. Yana ajiyeni ya bani 1500. Godiya na masa na shige shi kuma ya wuce.         Sani da tun fitowarsu gida yake biye da su daga can nesa da wajen ya samu waje yay parking. Kujerar motar ya kwantar abinsa yay kwanciyarsa ya buɗe data da sabuwar wayarsa daya siya jiya. Tunda yanzu babu aikin wahala ai kuma abinyi ya samu kenan. (🤣)       Ina shiga office ɗinmu na samu kira office ɗin MD. Takaici kamar nace bazanje ba amma dai na miƙe dan nasan hakan bai dace ba. Kamar yanda na saba sai da nai sallama ya bani izinin shiga sannan na shiga. A ciki na samu wata ma'aikaciyarmu mai suna Bashira, tunda na fara aiki a gidan nan nake ji ana faɗin son MD take kamar ta mutu. Amma shi yaƙi bata haɗin kai. Ina shiga da harararta na fara cin karo, ni saima taban dariya, amma dai banyi ba na ɗauke kaina kawai dan ba itace a gabana ba. Batare dana sauke face mask ɗin fuskana ba na ce, “Good morning Sir?”.         A sake ya amsa min da “How are you?”. Kamar bashi ne jiya ya gama tijareni harda korana a office ɗinsa ba. A taƙaice na ce, “Alhamdullah Sir ance kana kirana”.        “Eh zauna”.     Ban musaba na zauna saboda ganin cika da batsewar da Badhira keyi. Sai da na zauna a daƙile nace mata, “Morning”. Duk da tana sama dani. Aiko harzuƙa naga ta sake yi. Sai dai kafin tace wani abu MD ya tari numfashinta da faɗin, “Uhhm inaga na gama da ke ko Bashira, zaki iya tafiya zuwa anjima zan shigo department ɗin naku dan ina son ganin yanda zakuyi aikin”.        Kamar bazata muƙe ba sai kuma dai ta tashi a fusace tana cewa, “Okay”. Fuuu ta fita a office ɗin harda bugo ƙofa ji kake jifff. Daga ni har shi ƙofar muka kalla, ya girgiza kansa ni kuma na taɓe baki. Sai kuma ya kallan yana yin ƙaramar ƙwafa. “Sam bata da wayo. Ban cika son mace shasha mara aji irin haka ba”.     Ban tanka masa ba ni dai, dan babu abinda ya shallan sunfi kusa. Nima ban wuce ya zagan da abinda yafi haka ba tunda dai namiji yake. Ganin ban tanka ba shima sai ya saki batunta ya kama wani. Cikin lallashi ya ce, “Samraah sam banji daɗin abinda kikayi jiya ba ga babban mutum irin professor K/Mashi ba. Mutum ne mai mutunci da dattako. Yanda kike zatonsa sam ba haka yake ba. Kuma bada wata manufa ya mana wannan ƙyautar ba face dalilin abinda kikayi a wajen taron jikansa. Yaji daɗin yanda kika sakashi ya maganantu har ya amsa zaiyi hira da wannan gidan tvn namu. Maganar yin tasa hirar kuma bawai a jiya ne aka shiryata ba. Dama mun jima da tura masa goron gayyatarmu har a karo uku tun sanda akai wannan dogon yajin aikin na wata biyu daya shuɗe har yaya wata magana akan gwamnonin arewa datai matuƙar tada hazo amma yana bamu haƙuri saboda baya ƙasar, yana india ganin likita ne. Yanzu haka a jiyan kuma daga can nan ya sauka saboda taya jikansa murnar buɗe company da kuma amsa gayyatarmu. Kuskuren da aka samu dai shine da yace ba zaiyi hira da kowa ba sai ke saboda abinda kika yi a jiyan ya matuƙar ƙayatar da shi”.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒇𝒊𝒗𝒆_ .......A karon farko na sauke ajiyar zuciya. Sai kuma a hankali na ce, “Kayi haƙuri Sir an samu kuskuren fahimta ne kawai saboda ni bakamin bayanin komai ba. Kuma nima banƙi amsar ƙyautar tasa da wata manufa bane, kawai dai albashin da ake bani ya wadatar dani”.        “Humm kuma gashi ya dawo min da abinda ya bakin akan lallai na maida miki. Na kuma baki haƙuri tare da roƙonki kan ki amsa dan ALLAH.”     “Gaskiya bazan amsa ba Sir kuyi hakuri. Dan Yayana zai ɓata min rai matuƙa. Nima kuma a karan kaina ma nayima kaina alƙawari a gafarce ni”.        Shiru kawai yay yana kallona. Nasan mamakin taurin kaina yake yi. Dan har fuskarsa ta fara nuna jin haushi. Sai dai bai sake cewa komai ba akan batun face, “Okay ba damuwa. Sai batun mutuminki, a jiya PA ɗinsa ya turo mana takardar amsar gayyatar da kikai masa. Tare da bamu zaɓin lokaci amma kada mu wuce yau. Adai taƙaice yanzu haka ya tabbatar mana zai shigo kafin 11am, amma awa ɗaya kacal zai yi da mu. Dan haka yanzu zaki je ki kasance cikin shiri, nama su Tsanyawa magana akan su shirya kayan aiki da zauren da zaman zai kasance. A yanzu haka kuma sun fara in sha ALLAH”.           Har cikin raina sai da naji zantukansa na dukana. Amma sai na dake na amsa masa da to kawai. Shima bai sake cewa komai ba ya miƙamin takardar gabansa. “Ki nazarci wannan, idan kina da wata idea sai ki ƙara, nan da awa ɗaya ki kawo min na gani. Zaki iya tafiya”.        Zaram na miƙe kuwa na fice abina ko waiwayensa banyi ba. Zuciyata kuwa sai wani irin kai-kawo take. Ina fita kuma na dallama office ɗin harara. Ɗagowar da zanyi muka haɗa ido da Bashira, ashe tana tsaye a wajen bata tafi ba. Ko takanta banbi ba dan ba'itace a gabana ba nai wucewata a raina ina faɗin (Ballagaza kazar sakarai). Koda na koma office duk yanda naso samun damar tunani hakan bai yiwu ba. Dan su Ruƙayya tuni sun baibayeni da surutu akan ɗan ta'addan mutumin can mai kisan kai dako sunansa ban riƙe ba. Bana kuma fata ko ra'ayin riƙewar ma. Dan haka nafi maida hankali akan aikin gabana fiye da hirar tasu dan dama ba tofawa nake ba. A haka har lokacin da MD ya ban ya cika. Miƙewa nai na fita maida masa file ɗin. Yanda naga yana faman washe baki na tabbatar da abinda nai ɗin ya masa. Dan a take ya ɗaga waya yay kiran sauran wanda zamuyi aikin tare. Bayani ya sake mana ta yanda zamuyi komai ya ƙayatar ya kuma sake ɗaga kimar gidan namu. Ni sai ma naji kamar na makesa. Dan na fara saka MD a cikin jerin sunayen mutane mayun kuɗi. Jiba yanda yake rawar ƙafa tamkar zai ci da ka. Yana sallamar mu muka fice zuwa inda aka gyara domin gabatar da shirin. Makeup ɗin da akace na ɗanyi ƙi nai, sai ma shashsha musu ƙamshi nake famar yi. Sai da MD ya dinga lallashina sannan na ɗan sake saka fauda da ɗan lips gloss, daga haka ban sake bi takan komai ba na nema waje na zauna.        10:42am dai-dai aka sanar da isowar sa. Gaba ɗaya wanda ke a ɗakin MD yace mu fita a tarosa. Ko motsi banyi ba. Bamma da alamar hakan. Ganin MD na ƙoƙarin maido hankalinsa kaina nai saurin miƙewa nace zanyi fitsari. Babu yanda suka iya dani dole suka barni na fita zuwa bayi, su kuma suka fita tarbosa. Sai da na kwashe mintuna biyar da nake jin tabbacin duk ƙasaitarsa ya riga ya shigo sannan na koma. Har yanzu face mask ɗina na a fuskata dan haka baka isa gane yanayina ba. Tun kafin na ƙaraso na fara cin karo da gardawansa. Kallo ɗaya na musu na ɗauke kaina, dan ganinsu ma takaici yake sani. Yo banda rashin tawakkali miye na ajiyesu shi ba jami'in tsaro ba, shiba jinin sarauta ba, kawai dai giyar kuɗi da iyayi. Koda yake maybe al'adarsu ce hakan, tunda naga shima kakansa da nashi shekaran jiya. Baki na laɓe dai na ƙarasa shiga cikin takuna na nutsuwa da kowa kema kallon na yanga. Kaina tsaye na koma ɗakin da za'a gabatar da shirin, iya ma'aikatan mu kawai na samu a ciki suna ƙara gyagygyarawa. Ciki-ciki na sauke ajiyar zuciya ina mai ƙarasawa ciki. Ban tambayi kowa ya iso ko bai iso ɗin ba. Sai Usman ne yay tsulum yana faɗin, “Sam-G ki kasance cikin shiri baƙonmu na office ɗin MD yanzu haka. Nan da ƴan mintuna zasu shigo nan”.        Cikin taɓe baki na ce, “In dai ba mala'ikan mutuwa ne zai zo ba kuma dai Usman ai shirina yayi”.      Dariya ya sanya ƙasa-ƙasa. Ni kuma na cigaba da duba takardar hannuna. Goma da mintuna hamsin da biyar dai-dai Tsanyawa ya shigo yana sanar mana gasu nan tafe shi da MD. Sake kimtsawa kowa ya shigayi, banda ni kam, dan ko motsi banba daga yanda nake zaune balle na cire idanuna daga takardar dake a hannuna. Duk da face mask dana saka bai hana turarensa dukan hancina ba. Wannan dai fitina da yawa take, nikam bana rabe muku ɗayan biyu shima turaren na jinin tsafi ne shiyyasa yake danne ƙarfin duk wani turare idan mai shi yana waje. To nidai gaskiya ba yafewa zan ba, dan nawa kamfanin turaren suna iya nasu ƙoƙari suma. Jin yanda ɗakin yay tsitt kamar babu mutane yasa takaici sake kume ni. Chewing gum PA ɗin nan nasa ne ya fara shigowa, dole ne a kirasa chewing gum saboda koda yaushe dai yana manne da shi. Kusan a tare suka shigo da MD, sai wani rawar jiki yake da ƙanƙan da kai abin takaici. Duk wanda ke a zaune miƙewa sukayi, banda ni da takaicin MD ya sani ɗauke idona da nake musu kallon ƙasa-ƙasa da ban san mike faruwa ba. Ashe su Usman da ke zaune a inda nake duk sun tashi wai domin girmamawa.          “Samraah!”.     MD ya kirani ƙasa-ƙasa, banji ba dan haka Usman dake tsaye ta gefena ya ɗan bubbuga kujerar. Da farko sharesa nayi, dan nazata surutunsa ne ya tashi, ganin ya cigaba na ɗago ina harararsa. Idanunsa ya ɗan rumtse cikin yanayin matse fuska tare da mun nuni da MD ƙasa-ƙasa. Sai lokacin na lura da kallon da MD ɗin ke mun. Kowa na ɗakin nabi da kallo, ganinsu duk a tsaye shi kaɗaine zaune a inda za'a gudanar da program ɗin PA ɗinsa tsaye a kusa da shi ya ɗan ranƙwafa yana nuna masa abinda ke cikin tab ɗin hannunsa ya sani miƙewa batare dana sake kallon MD ba na ce, “Sorry Sir”.      Kansa kawai ya ɗan girgiza da mun nuni da can ɗin. Komai ban sake cewa ba na wuce inda zai kasance nawa mazaunin. Kujeru ne guda biyu kacal suna ɗan facing juna kaɗan, sai table a gabansu an ɗaura glass cup guda biyu masu ɗauke da ruwa, sai dai an rufe su da ɗan ƙananun fai-fai. Ta ƙasan ido na ɗan kallesu dan koda na zauna ban tanka musu ba ban kuma cire face mask ɗin fuska na ba. Yau ma dai suit ɗinne jikinsa milk colour, rigar ciki, belt da takalmansa ne kawai suka kasance coffee. Sai wani almurin agogo dake hannunsa da duk da ban san kuɗin agogo ba a kallo guda zaka san ba'a sayesa da kuɗi kaɗan ba. Dan coffee fatarsa ma kawai ka kalla kasan ba'a magana. Yau ma babu kitso bai kuma ɗaure gashin ba. Ya sakesa ne kawai baya ya sakko masa har akan kafaɗa kaɗan, akwai kuma coffee ɗan kunne ɗaya a kunnensa na dama yau ma ya manna. Sannan babu neck tie, maɓallan ma rigar cikin ta sama a buɗe suke.... Umarnin cire face mask ɗin fuskata da aka bani ya maidoni hayyacina. Cikin taɓe baki na janye idanuna dake cikin eyeglasses daga kansa ina yin abinda akace ɗin, dan lokacin fara gabatar da shirin yayi. Shima PA ɗin nasa wajen ya bari, yayinda ɗaya daga cikin abokan aikina ya ƙaraso gabansa, cike da ladabi ya maƙala masa abin magana a jikin jacket suit ɗinsa. Nima miƙomin yay na maƙala a jikin hijjab ɗina. Sai da aka tabbatar mun gama kimtsawa sannan aka ɗora camara a kanmu. MD ne cikin yanayin marairaicewa yay mun alamar na ɗan saki fusakata, jinai kamar na hararesa, amma na dake kawai cikin basarwa. Kamar bani ba, tuni yanayina ya koma zuwa sauƙaƙa fuska, sai da na kalla camara naima masu kallo sallama tare da gaisuwar barka da wannan lokaci da musu albishirin shiryawa tsaf domin ganin babban kamun da wannan shiri yayo musu yau a bazata sannan na juya garesa a yanayin jan class ɗina na ce, “Assalamu alaikum ranka ya daɗe”.        A hankali ya motsa lips ɗinsa ya amsa min da “Wa'alaikissalam” cikin muryar nan tasa a daƙile. Bazaka taɓa fahimtar kallona yake ko ba hakaba, saboda akwai eyeglasses mai duhu a idonsa. Yinai kamar ban damu da abinda yay ɗin ba nima, na cigaba da faɗin, “Wannan shiri na maka barka da zuwa, tare da nuna farin ciki matuƙa na cika alkawarin amsa gayyata a cikinsa a lokacin da kowa baiyi zato ba. Na tabbata hatta masu kallo ma zasu kasance cikin farin ciki maybe ma harda mamaki. Amma dai barkan ka da zuwa”.        Nan ma a takaice ya furta, “Barka. Tare da fatan alkairi ma kowa”.     (Ɗan rainin hankali) na faɗa a zuciyata. A zahiri kam na ce, “Masha ALLAH. To masu kallo, zan iya cewa duk sai ku sake matsowa gaban akwatinan talabijin naku, masu rediyo su ƙara sauti domin ji daga bakin babban baƙon namu.” Sake juyowa nai garesa ina faɗin, “Ko zamu iya sanin cikakken sunanka ranka ya daɗe?”.       Cike da wani salo da sake harɗe ƙafafunsa da yay crossing cikin motsa lips ɗinsa kaɗan ya ce, “Awwab El-Mu'azz K/Mashi. Sai dai Maash akafi sani”.     “Aiko nasan masu kallo zasu so sanin minene ma'anar Maash ɗin nan ranka ya daɗe?”.        Sai da ya bushi iska na wasu sakanni sannan yay wani ɗan murmushin gefen baki, a taƙaice ya ce, “Kwanar Mashi ne ainahin sunan tushena kenan, abokai suka maida shi Maash tun ina secondary school, daga nan kawai ya zama ana kirana da shi”.      “Uhhm Masha ALLAH. To ko zamu iya sanin wanene Maash a takaice. Dan wannan amsa ce da mutane suka jima suna son ji daga bakin ka amma basu samu damar hakan ba?”........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒔𝒊𝒙_ .......Ɗan jimm yay kamar bazai amsa ba, sai kuma ya kai hannu ya shafa ƙasunbarsa. Duk da glasses dake idonsa sosai nake jin kaifin idanun nasa yanzu kam a kaina. Amma sai na basar. Cikin yanayin rashin mafita da gurɓataccen harshensa ya bani amsa yana gwamutsa hausa da turanci sai na gyara masa ma wani lokacin.       “Awwab El-Mu'azz shine Maash. Asalin ɗan jihar Kano girman Lagos. Karatu zuwa matakin masters, wasu courses sun biyo baya duka dai a fanin kasuwanci. Ɓangaren karatun addini ma Alhamdullah. A yanzu haka business man”.        “Masha ALLAH. A yanda dai kake bayanin zabbirgewa, da daɗin saurare, sai dai a zahirance kafin aga Maash a haka nasan ansha gwagwarmaya bata wasa ba. Tare da ƙalubale kala-kala. Shin yaya ma akai ka fara kasuwanci?”.       “Business tamkar logo ne na family ɗin Ummie na. Kusan zan iya cewa na gada ne daga wajenta. Dan tun ina mitsitsi na nake ganin yanda take tsaye akan ƙafafunta ita da mahaifinta, grand father ɗin a kenan, sai hakan ya zaburar dani tashi akan wannan burin, kuma Alhamdullah yanzu an cimma buri. Batun ƙalubale kam ga duk wani rai mai numfashi koda bai tashi da nufin motsawa ba sai an fuskanta, amma Alhamdullah komai ya zama tarihi, dan ko yanzu haka an cimma burika da yawa harma da waɗanda ba'a tsara za'a cimmawa ba”.          “Gaskiya ne to Alhamdullah. Kafin yanzu Maash na kiran kansa ne kawai da suna bakano ɗan arewacin Nijeriya, sai dai mutane na ƙorafe-ƙorafe game da ko gidan kiwon tsuntsaye bai taɓa samarwa a arewacin ba duk da yanda ALLAH ya baka damar baza harkokin kasuwanci a duniya. Sannan ko cikakken Hausa ma bai iya ba. Shin ko Maash nada wani dalilin hakan?”.     “So babu wani dalili gaskiya. Kawai lokacin yin hakan ne baiyi ba, amma yanzu yayi ai gashi mun fara. Za kuma mu cigaba da yi in sha ALLAHU. Batun yare kuwa kowane ɗa kan fara tashi ne da yaran mahaifiya. Kasancewar mahaifiyata ba yarenta bane yasa na samu rauni a kansa, amma nasan ko yanzu zan iya fafatawa da kowa a kansa”.          Dariya maganarsa ta ƙarshe taban. Amma sai na dake na ce, “Kai ashe kace mu sake shiri bayan Companyn ƙera motoci akwai wasu ire-iren sa tafe ma kenan?”.     “Haka muke fata a cikin tsare-tsaren mu.”     “ALLAH ya cika buri”. A saman lips ya amsa min da “Amin”.     “Mi ya ja hankalin Maash buɗe katafaren Company irin haka a Kano da ba'a taɓa zato ba? Sannan ko Maash zai iya dawowa da rayuwarsa garin Kano gaba ɗaya?”..    “ALLAH ya rubuta anan ɗin ne za'a samar da shi. Idan ALLAH ya ƙaddara hakan kuma game da dawowa ɗin mizai hana”.        “Ko Maash nada aure?”.   “A kasuwa yake”. “A saka tallarsa kenan ko za'a samu wacce zata saya?”.       Fuska ya ɗan tsuke. A ɗan daƙile ya furta, “Ba'a gaji dani a gidanmu ba ai”.       (Wama zai so ka ɗan rainin wayo) na faɗa a zuciya. A fili kuwa sai na murmusa kawai na cigaba da faɗin, “Miyasa Maash baya son hira da ƴan jarida duk da suna ƙoƙarin ganin anyi hakan kodan tarin masoyansa da matasa irinsa da ake fatan su kallesa matsayin madubinsu?”.         Shiru yay baice komai ba, kusan minti ɗaya sannan ya furta, “Nothing”. A daƙile.    Nima a karan farko na ɗan kafesa da idanuna dake cikin glasses mai haske, dan sam ban gamsu ba. Amma sai MD dake bayan fage yay min nunin na barsa. Jinai kamar na dalla musu harara su duka. Amma na dake na cigaba da faɗin, “Wane kalar kaya Maash yafi so?”.         “Kowanne”.     “Abinci?”. “tuwo”. Wani kalar ɗan waro manyan idanuna nai waje a kansa. Shi kuma ya ɗan ɗauke kai cike da basarwa. Nima sai na ɗan basar ɗin kawai. Na cigaba da faɗin. “Wace shawara zaka bama matasa irinka dake tasowa?”.         “Su zama masu jajircewa, juriya akan duk abinda suka sa gaba, dan kayi karatu ba dole sai kayi aiki ba. Dan ka fara business ba dole sai kayi kuɗi kamar ƙyaftawar ido ba. Ka kasance mai Gaskiya akan komanka, neman zaɓin ALLAH da haƙuri akan halak duk ƙanƙantarsa. Ka kuma zama mai tarin wadatar zuci, dan in babu wadatar zuci ko zaka cika duniya da dukiya zakaita jin baka gamsu ba ne. Shaye-shaye baida wani amfani face maida matashi bayan baya a cikin al'umma. Shi iskanci ba'a koyansa, kowa da kake gani zai iya yi, zama mutumin kirki shike da matuƙar wahala, sai mu faɗama kammu gaskiya kafin duniya ta faɗa mana”.        “Masha ALLAH muna godiya da wannan shawara. Minene buri, ko nace shirin Maash na gaba?”.     “Maash nada tarin burika da shirye-shirye masu yawa da shi kansa bai san adadi ba. Amma manya daga cikinsu a dai yanzu sune samar da companys da zasuna fitar da abinci kowane nau'i in sha ALLAH. Zamu fara tsara komai a yanzu haka, muna fatan kuma zuwa ƙarshen shekarar nan komai ya zama ready”.       “Ko zamu iya sanin a ina wannan babban project ɗin zai kasance?”.     “Duka anan arewa ne in sha ALLAHU. Amma sai lokacin yayi za'a sani”.        “ALLAH ya cika buri”.     “Amin” ya amsa a taƙaice. “Mi Maash yafi so a rayuwarsa?”.            “My Parents”.       “Miye baya so?”. “Cin amana”. “ALLAH ya hanemu zama masu fuska biyu” na faɗa a yanayin kalma mai harshen damo ina ɗauke kaina daga kansa. Juyawa nai ga camara, fuskata ɗauke da ɗan murmushi na ce, “To masu kallonmu, gadai hira ta kwararo cike da daɗi, sai dai lokaci ya mana tsiyar tasa. Amma zance ku zama a cikin masu fatan wataran Maash ya sake zama a wannan kujerar domin amsa muku tarin tambayoyin dake a ranku da bamu kawo a wannan dandali ba yanzu saboda ƙarancin lokaci. Amma dai, ko a hakan ma mun gode, dan ALHERI TV ta kafa babban tarihi”. Sake juyawa nai garesa, na ce, “Ranka ya daɗe mun gode sosai da cika alkawari. Muna fatan ALLAH ya maidaka gida lafiya. Zaka iya yin sallama da masu kallo suma”.         Hannu kawai ya ɗaga yana mai sakin murmushi kaɗan ya ce, “Fatan alkairi”.      Ana ɗauke camara daga kammu ya wani sauke numfashi mai ƙarfi yana furzar da shi tare da jan siririn tsaki. Yinai kamar ma ban san da shi a wajen ba. Dan kafin ya tashi tuni na miƙe ni ina ɗaukar ruwan da aka ajiye mana da babu wanda yasha nabar wajen. Ban tsaya a ɗakin ba na fice gaba ɗaya. Office ɗinmu na koma. Bayan kamar mintuna sha biyar sai ga su Asiya sun shigo. Baibayeni sukai su duka har Usman da Khalid. Kowa na jinjina ƙoƙarin da nayi. Tare da nuna zumuɗinsu na fatan zuwan randa za'a saka shirin wa kowa dan su sake kallonsa a tsanake. Murmushi kawai nai musu nidai bance komai ba. Aikinmu muka cigaba dayi, har lokacin sallar Azhar yay muka fito gaba ɗaya. Bayan idar da salla kamar yanda muka saba na haɗu da Mansoor. Fita mukai restaurant ɗin kusa da ma'aikatar tamu cin abinci kamar kullum. Kusan a tare muka shiga da wani saurayi shima fuskarsa da fase mask. Bai mana magana ba bamu masa ba, kowa ya nema wajen zama ya zauna. Munci abincinmu cike da nishaɗi muna ƴar hirarmu. Bayan mun kammala muka fita. Mun koma office kan ayyukanmu. Banfi zaman mintuna biyar ba sai ga MD har cikin office ɗinmu Harun biye da shi. Duk miƙewa mukai domin girmamawa a garesa. Fuskarsa ɗauke da murmushi yay mana alamar mu zauna. Shima ya zauna a kujerar dake facing ɗina. “Sannu da ƙoƙari jarumarmu”. Ya faɗa idonsa a kaina. Sosai na waro nawa idanun dan mamakinsa. Kasa haƙuri nayi sai da na furta, “Jaruma kuma Sir, sai kace wata ƴar Film?”. “Ba'a Film kawai ake jarumta ba Samraah. A yau kinyi namijin ƙoƙari ƙwarai da gaske. Na tabbatar duk randa aka saki wannan hirar taku wa masu kallo ba ƙaramin tada hazo zatayi ba. Domin Maash yayi abinda bai taɓa kwatanta yi ba. Da ace kuma zan iya babu shakka sai na tambayesa ko miyyasa ya amince mana?. To amma ina, yana da wata irin kima da girma ga kwarjini mai saka shakkar koda kallonsa ne. Kin cancanci a kiraki kallabi tsakanin rawuna. Kuma in sha ALLAHU a dalilin wannan hirar zakiga babbar karramawa wa wannan gida dama duk wanda suka taimaka a ɗaukar shirin”. Tafi su Khalid suka shiga yi cikin ihu. Yayinda MD ke faman washe baki shima cikin nuna a nishaɗi yake. Ni dai na tsaya kawai ina kallonsu ne galala. Su dai murnarsu kawai sukeyi basu bi takaina ba, Asiya ce ma dai na ɗan ga yanayinta ya canja, da alama abinda suke ɗin bai mata ba, ko kuma zantukan MD ne suka zafeta oho mata. Sallama MD yay mana ya fita. Ni dai na sauke ajiyar zuciya kawai. Yayinda Ruƙayya ta rungumoni. Duka na kai mata kaɗan, ta sakan tana dariya bayan ta ja min hanci. Babu shiri nayi murmushi nima. Ruƙayya nada kirki sosai. Sannan halayenta na matuƙar burgeni. Shiyyasa a wasu lokutan sai naji kamar nace ma Yaya ya nema auranta dan ALLAH su sasanta. Amma ina tsorom halin maza kada yace bata masa ba. Duk da dai nasan babu wani namiji da zai kalli Ruƙayya yace bata masan ba. Dan ƙyaƙyƙyawar yarinya ce sosai. Tana da haske gata ƴar duma-duma abinta. Itama ta taɓa gaya min mahaifiyarta ta rasu a wajen haihuwarta. Kuma ita kaɗai ta bari, hannun kishiyar uwa ta tashi. Duk da bata fito ta faɗa min duka matsalarta ba na fahimci bata jin daɗin zaman gidansu, sai dai haƙurinta yasa bazaka taɓa gane hakan ba kai tsaye sai in har itace ta faɗa maka.......✍️          _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_ ........Tunda suka fito Hayatu ya zuba masa ido ta cikin mirror ɗin gaban motar, dan shi yana zaune ne a kusa da Tijjani driver. A hankali kamar mai ɗan jin shakka ya ce, “Sir ko zamu koma gida ne ka huta?”. Shiru kamar bazai tanka ba. Sai da ya mula dan kansa batare da ya buɗe idanunsa dake a rufe ba, ko gyara zaman ƙasaitar da yay ya motsa lips ɗinsa kaɗan. “Ba buƙata”. Ya faɗa a taƙaice. Kai kawai Hayatu ya jinjina yana mai haɗiye yawu. Kai tsaye Company suka nufa. Dan akwai zaman meeting da zasuyi sakamakon fara ɗaukar ma'aikata da za'ayi a gobe in sha ALLAHU. Sun samu duk wanda ake buƙatar gani a zaman meeting ɗin yazo. Tunda aka buɗe masa mota kuma ya fita kowa keta ƙoƙarin gaida shi cikin girmamawa. Hannu kawai yake ɗaga musu da bin yanayin wajen da kallo ƙasa-ƙasa. Hatta da turawa da Chaines ɗin da zasu jagoranci aiki a companyn girmamashi sukeyi. Kai tsaye hall ɗin da meeting ɗin zai gunada suka nufa. Wajene da akai matuƙar tsarawa da ƙawatawa. Sai da ya zauna a babbar kujerar dake tsakiyar dogon tables ɗin sannan suma kowa ya zauna. Ya ƙare musu kallo ƙasa-ƙasa ta cikin gilashinsa ɗaya bayan ɗaya kafin suka fara gudanar da abinda ya tarasu.. ★ A matuƙar gajiye liƙis suka bar Company bayan sallar la'asar. Koda suka isa gida sun samu baƙonsa Abubakar yazo. Saboda yanda yake jinsa a takure bai iya ganawa da shi ba ma ya shige bedroom. Wanka ya farayi sannan ya ɗan kwanta. Tabbacin ya gaji sosai cikin ƙanƙanin lokaci barci mai nauyi yay awon gaba da shi kuwa. Bai fito ba sai lokacin sallar magrib, sai da kuma akai isha'i ya dawo gidan. A sannan ne yay ɗan zaman awa guda da Abubakar da Hayatu. Suna kammalawa ya bama Hayatu umarnin su shirya jirgin sha biyu na daren yau ɗin nan zasu bi zuwa Lagos. Hakan ba sabon abu bane a gare su. Dan shi duk sanda abu ya kaɗa masa yinsa kawai yake yi, ko dan jirgin nasa ne na kansa yake hakan oho masa . Tunda ma har aka tsaida time ɗin tafiyar yasan Juliet ita ta sani, amma duk da haka bayan ya sanar da guards da Tijjani su shirya sai ya nufi sashen da take. Hayatu na gab da shiga falon wayarsa tai tsuwwa alamar shigowar saƙo. Baibi takanta ba ya ƙarasa. A falo ya samu Juliet ɗin tana waya. Ganinsa yasa ta katse sukai maganar da zasuyi ya fito. Shima nasa masaukin ya nufa domin kimtsawa. Duk da dai akwai ɗan sauran lokaci ma. Daga aljihu ya cire wayarsa da nufin ajiyewa sai kuma ya fasa saboda tuna shigowar saƙon ɗazun.        “What!” ya faɗa da ƙarfi, sai kuma ya miƙe da saurinsa cikin sassarfa ya fice. Kai tsaye sashen ogan nasu ya koma. Sallama ɗaya yay batare da jiran izini ba ya afka ciki. Dai-dai nan kuma Maash ke fitowa da ga bedroom ɗinsa kunnen sa manne da bluetooth alamar waya yake yi, yanda ya tsuke fuska matuƙa zai tabbatar maka koma da waye yake yinta bada daɗin rai bane. Kallo ɗaya yay ma Hayatu daya shigo kamar an korosa ya ɗauke idonsa. Cikin kujera ya kai yana wani kalar cije lips ɗinsa. Sai kuma kamar a fusace ya furta, “Nifa ba fushi nake ba Paa. Maganar yarinyar nan kuma nace a barta bana so. Ni ban taɓa cewa ai ina ra'ayin zama da ita ba, kuma ban taɓa cemata ina sonta ba”.       Ɗan shiru yay alamar yana saurare, sai kuma ya sake ɓata fuska a yanayin shagwaɓa ya sake cewa, “Paa Please mana. Understand me.”      Sai kuma ya sake yin shiru. Kusan minti ɗaya ya ce, “Okay naji, amma ni daga nan zan wuce Finland ne, bazan dawo ta Lagos ba. Kwana shida zanyi kawai in sha ALLAH”.       Guntun murmushi ya saki kaɗan, sai kuma a hankali ya ce, “I love you too. Bye ka gaida Ummie da Mamma.” daga haka ya cire bluetooth ɗin yana maida hankalinsa kan Hayatu. Hayatu da dama kamar a ɗofane yake a saman wuta yay wata zabura zuwa gabansa. Cikin rawar hannu ya miƙa masa wayar yana faɗin, “Sir yarinyar nan ce fa ta sake turo saƙo ta number na. Ban san taya ta samu ba, ko yau da mukaje office ɗinsu ne?”.       Komai baice ba ya amshi wayar. Kasancewar da turanci aka rubata text message ɗin yasa ya fahimci komai. Ya jima bai motsa ba ya ƙurama wayar kawai cat eyes ɗin shi, sai dai fuskarsa ta sake komawa wani bala'in kicin-kicin har blue ɗin cikin idanunsa na ƙoƙarin ɓacewa. Hayatu ne ya katse shirun da faɗin, “Wlhy Sir al'amarin yarinyar nan mamaki yake bani, na jima banga mace mai busashiyar zuciya irinta ba. Just small girl ɗin nan wai tasan yin irin wannan ta'addacin haka. Jiba yau yanda take wani basarwa da shan ƙamshi fa. Ni wlhy dan kawai kace a barta ne ai. Amma har ita wacece da bazamu sa a tattaro mana kaf zuri'ar gidansu ba taga ƙaryar tsagerancin nata. Haba ita wacece da zata zauna tana rainama mutane hankali. Kawai na kira Sani a daren nan ya kawo mana ita gidan nan a amshi wayar tata a gabanta mu goge video ɗin sannan mu danƙata hannun hukuma, muda muke da makami ma a kanta, dan biyowa ta bayan gida fa tai akan hira dakai har yanzu ba'a daina cecekuce a kansa ba a media, wani abun ma nasan sai randa aka saki hirar, tabbacin mutane da yawa na asiri tazo da shi wajen har ka yarda ka amsa matan zai sake gitowa”.      Shi gaba ɗaya ma surutun Hayatun saka masa ciwon kai yake. Dan haka ya wurga masa wani kallon da ya sakashi nutsuwa, tare da jan bakinsa ya tsuke. Shiru falon ya sake ɗauka kowa na cuɗawa da kwancewa a cikinsu. Kafin shi ya miƙama Hayatu wayar yana faɗin, “Ba buƙatar mata komai a yanzu. Ina son ganin iya gudun ruwanta. Ka amsa mata da za'a bata 500m ɗin, amma a ina za'a haɗu da ita ta bada recording ɗin”.           “Amma Sir.....”      Hannu ya ɗaga masa, a daƙile ya ce, “Na gama magana”.     Yawu mai ɗaci Hayatu ya haɗiye. Sai kuma ya jinjina kansa cikin girmamawa ya ce, “Okay Sir, in sha ALLAH za'ayi yanda kace. Na barka lafiya”. Daga haka ya juya ya fice. Ta gefen ido Marsh ya bisa da kallo. Sai kuma yay wani kalar furzar da iska yana maida kansa a kujera ya kwantare tare da lumshe idanunsa a hankali. Shi kaɗai yasan mi yake ji a ransa game da yarinyar nan. Ya fahimci lallai bata fahimci a ramin da take neman jefa ƙafarta ba. Amma zai bata lokaci ta gama nata kalar ƙaramin wasan kafin ya fara buga babban game da sai tayi dana sanin saninsa a rayuwarta a kanta. Idan ita ƙaramar ƴar iskar layi ce, zai tabbatar mata shi na duniya ne baki ɗaya, dan ba neman kuɗi kawai ya iya ba harda cin uban duk wanda ya shiga sabgarsa. Ko abubuwan data dinga yi yau duk a rubuce suke a brain ɗin, ya fahimci tanada taurin kai da tsageranci. Duk zai sauke mata su kuwa nan bada jimawa ba.       Ya jima a wajen zaune har Hayatu ya dawo ɗauke da abincin da Sani yayo order. Amma sai yace bazai ci ba. Ya haɗa masa coffee kawai. Umarninsa Hayatu yabi. Ya kawo masa coffee amma ya haɗo da biscuits mai daɗi. Dan yasan waɗan nan sune kalar ciye-ciyen da ogan nasu yafi so a rayuwarsa. Shiyyasa a duk inda yake baka rabashi da kalolin biscuits da chocolates kala-kala masu shegen daɗi. Sabone tun na ƙuruciya ya riga ya kamashi. Sake fita Hayatun yay ya barsa, shi kuma ya maida hankalinsa ga tv yana kallon film ɗin da sukeyi yana shan coffee ɗinsa da biscuit ɗin kamar baya so. Koda ya kammala zamansa ya cigaba dayi har sai da film ɗin ya ƙare sannan ya shige ciki. Maimakon kwanciya bathroom ya faɗa, ya haɗa ruwa mai ɗumi cikin bathtub tare da haɗa kayan ƙamshi kala-kala a ruwan sannan ya shiga ciki. Sai da yay minti talatin cur ruwan na ratsashi da miƙar masa da kowace gaɓa sannan ya fito ya shiga wajen wanka ya ɗauraye jikinsa. Bayan ya fito salla ya fara gabatarwa tare da shafa'i da wutiri sannan ya shiga shiri. Yayi ƙyau sosai cikin shigar tasa tamkar ka sacesa ka gudu. Ga wani uban ƙamshi na tashi uwa kamfanin haɗa turare kamar ba dare ba. Sumar nan tasha gyara daka gansa kasan ya haɗa jini da masu jajayen kunne. Hakama kwantaccen gashin sajensa sai walƙiya yake gashi kwance luf-luf ya sake fidda taswurar doguwar fuskarsa. Sai da ya tabbatar komai ya masa yanda yake buƙata sannan ya fito cikin nutsuwarsa da takunsa na tsayayyen namiji. Baiyi mamakin ganin Hayatu a falon ba. Dan duk inda aka gansa dolene aga Hayatun. Duk da yana jin idonsa a kansa bai kallesa ba. Hakan yasa Hayatu ɗauke idonsa shima a ransa yana kirari wa UBANGIJI mahaliccin wannan ƙyaƙyƙyawar halitta, gaskiya dole ma aso mai ƙyau, dan ko shi dake a namiji, kuma ana yawan sanar masa shima ɗin ƙyaƙyƙyawane har ga ALLAH ogansa na birgesa. Dan mutum ne daya san hakkin tsara ado. Ya iya tsara saka sutura ta zauna ɗam ya haskata kuma tamkar dan shi kaɗai ake saƙa kaya irinsu. Ganin zai ɗago da sauri ya wuce sumu-sumu zuwa bedroom dan ya kashe komai ya gyara kuma abinda ya ɓata tunda basu san ranar dawowarsu Kano ɗin ba kuma. Suda suke kullum a tafiye-tafiye kamar ƴan sama jannati.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_ .......Kamar ko yaushe yau ma Mansoor ne ya maida ni gida, koda na shiga na samu gidan tsitt. Banbi takan kowaba na shige ɗaki, auta na samu yana barci, ga books ɗinsa a gefensa barbaje alamar homework yake barcin ya kwashesa. Ɗagashi nai na maida kan katifa. Sannan na tattare books ɗin na ajiye masa gefe bayan na duba abinda yake. Yaron akwai brain, inba ni ba babu mai zama damuwar koya masa homework, sai idan Abba. Wani lokacin ma sai kika yayi da kansa kafin ma na dawo, sai dai na ɗan masa gyararraki kawai. Wanka nai ƙoƙarin shiga, sai dai bayin duk an ɓata shi, nasan Bibaa ce zatai wannan aikin ba wani ba. Na rasa mike damun kan yarinyar nan, amma zan koya mata hankali. Tanada ɗakinta ita kaɗai amma tsabar shaiɗanci tace tsoro take ji a can, shine Abba yace ta dawo nan mu zauna wai sai ta ƙara girma. Da farko na ɗauka haka ɗinne, sai daga baya na fahimci Mom ce ta sakata yin hakan dan ta dinga ɗaukar rahoton duk motsina tana kai musu. Tun wani lokaci da naji tana faɗama Mom wayar da mukai da Mansoor nagane hakan. Bayin na sake gyarawa sannan nai wankan. Harna fito na gyara jikina banji motsin kowa ba. Ba'a wani ɓata falonba yau sosai, dan haka na wuce kitchen. Shi kam yana nan jibge da kayan wanke-wanke tun daga kofunan kalacin safe har na rana da sukaci. Kaina na girgiza ina mai jin tausayin Bibaa da Baby a rayuwa. Dan ita Mom gani take gata take musu bata san kashe musu rayuwar take ba, haka kullum da rayuwar take a gidan, idan nai aikin safe na fita babu abinda suke kaudawa har sai na dawo na sake yi, badan nima na zama jan wuya ba abincin rana ma sai na musu na saka a kula. Sai da na nuna musu nima tsagerar kaina ce sannan, shiyyasa kullum basu da abincin rana a gidan sai taliya ko cus-cus ko macaroni, indomie. Sai idan akwai stew ne zakiga sun dafa farar shinkafa. Stew ɗin kuma zakiga dole nice zanyita, Mom taƙi yarda a ajiye mai aiki wai ita kishi, randa nayi aure to naga ubanda zai zo ya musu. Kwanikan na fara tattarewa na wanke, ƙafafuna duk sunyi tsami saboda tsaiwa. Haka dai na daure na kammala na maida komai muhalinsa sannan shima kitchen ɗin na shiga gyaransa. Ƙaramar indomie na dafa guda biyu, na raba biyu naci tawa anan na juyema auta tasa a plate. Har lokacin babu wanda ya dawo, mamaki ya sake kamani da tunanin ina sukaje haka ne?.       Har akai sallar magrib sai mu kaɗai a gidan. Sai bayan an idar Abba ya shigo. Fita mukai ni da auta daya tashi muka gaishesa. Na wuce na kawo masa ruwa na koma ɗaki abina na barsu anan falo. Sun fita sallar isha'i nima zan kabbara tawa naji hayaniyar shigowar su Mom. Banbi takansu ba na tada sallata. Sai da nai har shafa'i da wutiri sannan na fito musu sannu da dawowa. Kaya na tarar barbaje a falon kashi-kashi. Na sakawa dana kwalliya harda na ciye-ciye alamar dai daga kasuwa suke. Ganin hankalinsu baya kaina dan ko gaisuwar ma da kai Mom ta amsa min na juya na koma abina ina mamaki, dan tabbas da kuɗin Yaya na jiya akai wannan sayayyar kenan. Jinai raina ya ɓaci matuƙa, dan haka na fito na wucesu. Yanzun ma hankalinsu babu alamar yana kaina. Ta ihun murnar kayansu suke kawai. Ɗakin Yaya Musaddiq na nufa, yana tsaye da alama yanzu ne yake dawowa massalaci. Ganina rai ɓace ya sashi faɗin, “Jikin ne?”. Kaina na girgiza masa ina kaiwa zaune. Cikin zafin rai na ce, “Wlhy Yaya zancen kuɗin sarƙar nan shirine kawai. Ko kasan matar can yau kasuwa suka shiga ita da ƴaƴan nata gasu can sun baje kaya a falo kamar za'a buɗe kanti. Kasan kuma babu yanda za'ai hakan ta faru Mom ta iya kashe kuɗin sarƙar nan a banza haka da gaskiya ne”.        Murmushi mai sanyi Yaya Musaddiq yay hana kaiwa zaune kusa dani. Cikin sauƙaƙa murya tare da riƙo hannuna cikin nashi ya furta, “Cool down sweetheart. Sune a ƙasa ai. Bakiji shata na faɗin ku gargaɗi mai gina ramin mugunta ba. Ni nasan dama koda an ɗauki sarƙar ma bata kai ta kuɗin data faɗa ɗin ba. Amma ba komai ALLAH zai bamu wasu. Yanzu ma Abba ya bar ɗakin nan”.        “Miya faru ya shigo?”. Na faɗa cikin mamaki tunda nasan dole akwai dalili. Hannuna ya saki yana miƙewa da ɗan taɓe bakinsa. Ya zare jallabiyarsa ya ajiye sannan ya koma ya zauna dan jikinsa akwai dogon wando da t-shirt fara. “Yazo ya sameni akan wai tunda yaga inada kuɗi ni ne ya kamata na miki komai na aure. Dan shi gaskiya yana a cikin damuwar rashin kuɗi. Saboda hakane ma yaƙi yarda su tsaida rana a randa iyayen Mansoor suka zo. Amma da yasan har inada wannan kuɗin haka aida an kammala komai. Dan haka zai kirasu suzo weekend ɗin nan a tsaida ɗin. Na kuma bashi aron 200k zuwa ɗan wani lokaci zai bani..”        “Kuttt! Amma mutumin nan ko! Wai mike damun Abban nan ne?. Dama ko bai faɗaba waye ke jiran wani abu da ga garesa mtsowww aikin banza. Sannan kuma bashin ka amsa zaka bashi Yaya?”.     Murmushi Yaya Musaddiq ya saki mai haɗe da dariya, sai kuma ya girgiza kansa. “Kai wannan yarinya masifaffiya ce ke wlhy, wanda basu sanki bane kawai suke miki kallon mai haƙuri. Ni ALLAH har ma na fara tausayin Mansoor bawan ALLAH shi gashi da sauƙin halin tsiya”.     Baki na tura ina faɗin, “Kai Yaya nice masifaffiyar?”.       “Ta bugawa ma kuwa a jarida kandala. Wani lokacin da idan kina abu sai naga kamar ma kece Yayar tawa. Shiyyasa Hafizzullah ke cewa da kece Mamanmu da mun shiga uku”.       Dariya na ƙyalƙyale da shi. Na ce, “Masherancine yaron nan ai. Dan ALLAH Yaya weekend ɗin nan muje mu gansa tunda wancan ya shuɗe. ALLAH ina kewarsa”.         “Karki damu zamuje in sha ALLAHU. Dan na kammala masa ma siyayyarsa.”      Cike da farin ciki nace “Yauwa Yayanmu, kuma Babanmu. Yanzu dai yaya mi kacema Abban?”.        Sai da yay murmushi ya ce, “Mizan ce masa kuwa Samraah. Na gaya masa kuɗin dana bama Mom ɗin jiya ne kaɗai dama a wajena, sai abinda ya rage baifi saura dubu arba'in ba nama cire wani abu a ciki na haɗama Hafizzullah provision. Dama na tara wancan kuɗinne dan na basa shi da Mom ɗin su rage hidimar biki. Ga kuma abinda ya faru yanzu. Ina gaya miki sai kawai ya hauni da faɗa. Wai to wlhy sai nasan inda zan nemo wasu kuwa. Dan shi dai baida wani kuɗin yin hidimar nan bai kuma da hanyar samunsu. Inba hakaba kuwa sai dai a kaiki gidan mijin a haka.. inada yake shiga dai bata nan yake fita ba.”        Wata shegiyar dariya na bushe da ita harda kwanciya ina hawaye. Yaya Musaddiq kuwa yay sagale yana kallona. Sai da yaga dariyar tawa ta tasamma ta hauka sannan ya ce, “Samraah kin samu motsuwar kai ne?”.       “Babu wani motsuwar kai wlhy Yaya. Show ɗin ne yay matuƙar burgeni. Su Abba an lallaɓo aci banza. Banza bata samu ba, shine ya ƙare da borin kunya. To waye ya faɗa masa na damu a kaini da kayan ɗaki? Ko cokali ma kada su saya waye zaiji kunya”.         “Shirme maganinka ALLAH kenan”. Yaya Musaddiq ya faɗa yana girgiza kansa. Da sauri na ce, “Yaya gaskiya fa na faɗa. Ni wlhy ban damu ba amin kayan ɗaki ko a kar ayin. Badai muna son junanmu ni da Mansoor ɗina ba”.      “Baki da kunya, a gabana kike cewa kuna son juna”.     Hannu nasa na rufe fuskata ina dariya. Shima sai ya shiga tayani...         Washe gari koda na kammala aikina na shirya na fito na samu Abba a falo na gaishesa bai amsa min ba. Ko'a kwalar rigata nai ficewata. Yaya ga ɗaukan muka wuce ina bashi labari ina dariya. Shi kam murmushi kawai yayi yace “ALLAH ya ƙyauta”. Haka rayuwa ta cigaba da tafiya gidan Abba babu daɗi sai haƙurin UBANGIJI kawai. Yayinda a waje aiki ke caja kai kuma. Kamar yanda mukai shiri ranar asabar muka tafi Katsina ganin Hafizzullah. Ƙiri-ƙiri Mom ta nuna baƙin cikinta akan hakan. Ta shiga zuga Abba wai ya hanamu zuwa. Sai dai Yaya ya nuna musu babu abinda zai sakamu fasawar. Haka dai muka tafi Mom na banbaminta na rashin gaskiya. Hafizzullah yayi matuƙar farin ciki da ganinmu. Dan harda kukansa na murna. Ya rame saboda karatu, naita tsokanarsa nikuwa muna faɗanmu da muka saba. Tare da shi muka yini. Da zamu wuce masauki kuma ya bimu akan shi tare damu zai kwana. Nan ma raba dare mukai muna hira kafin su koma ɗakin Yaya Musaddiq su kwanta ni kuma nai kwanciyata ni kaɗai muka sha waya da Mansoor dake bani labarin an shirya komai tsaf gobe in sha ALLAHU za'a tsaida date. Jinai duk wani iri, amma a ƙasan raina ina farin ciki da hakan. Koba komai ai zan samu ƴancin kaina. Na kuma samawa ƴan uwana. Dan insha ALLAHU Hafizzullah gidana zai koma, Yaya kuwa zan cigaba da dagewa akan yay aure..........✍️           _Kandala ta malam Mansoor 😘_ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒘𝒆𝒏𝒕𝒚 𝒏𝒊𝒏𝒆_ ........Washe gari kamar yanda Mansoor ya faɗa muna a hanyar dawowa gida ya turamin saƙo na jerarrun kalaman godiya ga ALLAH. Tare da sanar min an tsaida wata ɗaya kacal, nanda kwana talatin in sha ALLAHU na zama mallakinsa. A gidansa zanyi azumin watan Ramadan. Duk da naji farin ciki ban maida masa reply ba, dan ina cikin mood mara daɗi na rabuwa da Hafizzullah. Shima mun barosa harda hawayensa. Munko samu gida cike da kayan sweet, biscuits da drinks a falo. Harda su goro sai akwatina guda biyu. Yanda babu wanda yay min magana akan kayan nima banma kowa ba. Sai auta ne ke faɗamin Uncle Mansoor ya gaya masa kayana ne. Sai kuma habaicin da Baby keta saki ranta a ɓace. A kallo ɗaya da nai mata kuma na fahimci tasha kuka. Ban kulata ba dan ba itace a gabana ba. Washe gari Monday na wuce aiki da wuri. Bayan mun dawo na tarar da Gwaggo Gudidi tazo daga Dawanau. Kakace a wajenmu, dan ƙanwar kakarmu ce, mahaifiyar su Abba da mamanmu kenan. Ba sosai take zuwa gidan ba saboda wulaƙancin da Mom ke musu. Mu kuma Abba baya barinmu zuwa wajenta, garama Yaya yanzu daya mallaki hankalin kansa yana zuwa abinsa. Yanzun ma shine ya kirata ya gaya mata komai ganin Abba baida niyyar saka danginsa ko ɗaya a batun auren nawa. Ƴan Gwarzo kuwa sun kwashi nasu kason kayan da za'a rabama mutane sun wuce dasu tun jiyan, dan bamu samesu ma a gidan ba. Nayi murna ƙwarai da ganin Gwaggo Gudidi. A take na shiga hidima da ita dan naga babu alamar ko abincin kirki ma an bata. Duk da hararar da Mom ke mun banbi takanta ba na shiga hidima da kakarmu. Bayan sallar isha'i kuma Yaya ya sayo mata kayan ƙwaɗayi yazo ga zauna muka sha hira. Dan dole Abba ma yazo ya zauna akayi da shi shima. Mom da ƴaƴanta kuwa kowa yay shigewarsa ɗaki sai Auta da uwar gulma Bibaa kawai a wajen. Bamu tashi a falon ba sai sha biyu. Abba ko tun sha ɗaya matarsa tazo ta tasashi suka shige ko kunyar Gwaggo Gudidi bata ji ba balle mu ƴaƴa. Shimfiɗata na barma Gwaggo, dan Yaya Musaddiq ya kawo mata babban bargonsa. Zan kwanta a ƙasa tace na hawo kan bargon. Badan naso hakan ba na hau dole. Sabuwar hira muka buɗe da ita har sai ɗaya sannan barci ya kwasheta. Niko alwala na tashi nayi nai nafilfilina kamar yanda na saba sannan na kwanta. Hakan kuma bai hanani tashi uku da rabi ba na shiga ayyukana. Kafin kace mi na kammala, dan har abinci naima Gwaggo na saka mata a kula nakai ɗaki dan nasan ba lallai da rana a bata na kirki ba. Gashi ban dawoba lokacin. Kalacin ma isashe na ɗiba mata. Itako tanata mitar yanda nake wannan uban aiki ga fitar safe kuma. Ni dai bance komai ba face murmushi kawai. Yau kam Yaya Musaddiq ya shigo gidan domin gaisheta. Ya ajiye mata kayan shayi da ƙaton bread ɗin ta harda soyayyan ƙwai. Albarka ta dinga saka mana sannan mukai mata sallama muka wuce dan kar mu makara. Gwaggo Gudidi itace ta raba komai na kayan sa ranar nan. Har maƙwafta sai da tasa Auta ya kai ma kowa gida-gida. Sannan dangin su ta ƙulla na kowa daki-daki. Wanda ke anan cikin Kano ta saka Yaya Musaddiq ya kaita ta kai ma kowa. Na Gwarzo ma tare sukaje takai duk na ɓangaren danginsu dai. Yaya Musaddiq ma da Hafizzullah ta ɗiba musu. Nima komai sai da ta ɗiba min. Hakama jama'ar gidan kowa da nashi. Kuma kowa zai iya rabama abokan arziƙinsa idan yaso. Amma sai Mom tai biris da nata anan falo har Gwaggo ta wuce bata ɗauke ba daga ita har ƴaƴanta. Abba dai ganin Gwaggon yasa shi zama ya ƙuƙƙula ya fita dasu wai zai rabama abokansa da ƴan wajen aikinsu. Ya raba ko bai raba ba oho masa.        A ranar da nakai ma ƴan office ɗinmu kowa ya sake sanin alaƙata da Mansoor, dan wasu basu ɗauka gaske soyayya muke ba saboda yanda muke komai cikin taku. MD kuwa ai kamar zai mutu. Dan masifa yayta zubama kowa a wannan yinin babu gaira babu sabar. Har dai ƴan uwana ma'aikata suka fahimci kishi yake yi. Ni dariyama ya bani wlhy. Mansoor kam yaji daɗin abinda nayi, dan bai ɓoye ba sai da ya sanar min. Murmushi kawai na masa nidai. Bayan an tashi aiki ya buƙaci kaini naga aikin gida da ake ƙarasawa. Amma sai nace masa ba yau ba ya bari weekend zai fi. Shima ya yarda da shawarar tawa. Dan haka ya maidani gida. A ranar ne kuma na fahimci wata farar mota na binmu a baya. Duk da naji tsoro sai banyi magana ba, nace bari dai na tabbatar. Ganin munzo titin shiga layinmu motar ta wuce yasa na sauke ajiyar zuciya har Mansoor na kallona.      “Lafiya irin wannan ajiyar zuciya haka kamar wadda nai shirin sacewa. Ko tsoro kike kada na wuce dake ne?”.         “Ai kaima bazaka fara hakan ba sai an baka”. Na faɗa cikin kauda kai ina murmushi. Shima ƙaramar dariya yay da sake faɗin, “Hakane. Amma da zama a taimaka a banin yau zanfi kowa farin ciki. Maybe ma na ƙara samun ƙarfin aikin yanda ya kamata”.       “Humm” kawai nace na buɗe motar na fice ina murmushi. Godiya na masa kamar kullum. Yanata son mu haɗa ido amma naƙi yarda da hakan. Sai ma na wuce da sauri na shige gida abina. Amma na maƙale jikin gate ina leƙansa. Yaja kusan minti ɗaya idonsa a gate ɗin fuskarsa da murmushi kafin ya tada motar ya wuce...       ★★★    Abubuwa kullum ƙara tsamari suke a gidanmu. Dan kullum al'amarin Mom da yaranta gaba yake yi. Ina sake samun tsangwama da hantara fiye da baya a yanzu sakamakon wannan batun auren. Yayinda Baby ta fito da maitarta akan Mansoor yanzu. Shi kansa ya fara nuna min tana matsa masa. Ashe tun da can ma da bata fiddo abubuwanta fili game da shi akwai abinda take shakka daga garesa, na kuma fahimci wani babban sirrinta ne ya sani duk da yaƙi fitowa fili ya faɗa min.         Sam ba'a wani shiri irin na aurar da ƴa a gidan, musamman ma mace da bikinta ke da yawan hidima. Ko kaɗan hakan baya damuna. Dan nasan Yaya Musaddiq tsaye yake akan al'amurina ta bayan fage. Dan yanzu kusan duk sati zakiga Gwaggo Gudidi tazo mana. Da alama akwai abinda sukeyi ita da Yayan. Duk da madai ashe shi Mansoor ya samu Yaya akan shi baya buƙatar komai na gida duk zai zuba. Ni shaidace akan abinda ya faɗa ɗin domin ya kaini naga gida. A randa mukaje ɗin kuma na sake kama motar nan na binmu. Hankalina ya tashi fiye da ranar, amma nai jarumtar dannewa saboda kada na tada hankalin kowa. Nayi kuma alƙawarin saka ido sosai dan na tabbatar shin da gasken binmu ake kokuwa zargina ne kawai. Tun daga wannan lokacin na saka ido fiye da koda yaushe. Babbar magana kenan wai ɗan sanda yaga gawar soja, nako tabbatar bibiyata akeyi ɗin. Dan harna haddace Number motar duk da dai mai ita kan canja ne kusan da kala uku, sannan ita kanta motar wani lokacin bada ita ake bina ba da napep ne. Al'amarin ƙuruciya irin nawa da wauta, maimakon na sanarma ko Yaya ne sai nai tunanin kada na tada masa da hankali, gara na fara sanin wanda ke bibiyar tawa dai. Wannan ɗammara dana ɗauka tasa na fara ƙin daina bin yaya na koma shiga napep. Hakama Mansoor wataran sai na ƙi biyosa, ina amfani da yanayin da yake ciki na busy yanzu akan shirin biki. A ranar farko dana fara yin ƙundun balar tarar motar nan sai aka gudu. Karo na biyu ma haka. Ganin haka na sake himma dan a ganina tsorona ake ji. A karo na uku na haɗa kai da ƴan ƙato da goran anguwarmu a ɓoye akan idan ma fita su bini a baya. Na basu numbers na motar da ake amfani da su har kala uku. Abin zai baku mamaki, dan kamar mai motar nan ya fahimci abinda nake ƙullawa ranar sai bai bini ba. Tsahon kwana uku haka na ƙara yarda yaji tsorone na sallami ƴan ƙato da goran. Sai me a randa na sallamesu a ranar na cigaba da ganin motar kuma. Raina yakai ƙololuwar ɓaci. Na fara zargin MD ne kemin hakan ko kuma Abba ko Mom ko Baby. Kai har Mansoor sai da na zarga, to sai dai kuma shi danmi zai sa a bibiyan bayan kullum muna tare. (Bincike) zuciyata ta ayyana min. Ban gamsuba, dan in bincikene ai iyayensa ne zasusa ai musu. Sannan bata wannan hanyar ba, anguwarmu zasu je. Amma duk da haka sai nace bari na gwada kowannensu. Da Baby da Mom na fara. Sai banga wata alamar hakan ba daga garesu. Shima Abba haka. Sai kawai na koma kan Mansoor. A randa na taresa da zancen ina magana cikin tsiwa kan basai fa yasa ana bibiyata ba zai san halina. Idan bincike yake son yi a kaina yazo ga ƴan anguwar dana tashi cikinsu tun ƙuruciya har girma mana. Amma sakawa ana bibiyata kamar son firgitar da ni ne. Tare da nuna rashin aminci a tsakanina da shi. Sagale yay yana kallona da mamaki, sai dai bai iya cewa komai ba harna fita a fusace. To ashe daga nan bai zame ko ina ba sai wajen Yaya Musaddiq suka tattauna akan hakan. Lokacin da Yaya Musaddiq ya dawo aiki yay kirana ɗakinsa.......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝑻𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚_ .......Da faɗa ya faramin tare da turkeni kan saina faɗa masa dalilina na jifan Mansoor ɗin da waɗan nan kalaman. Da farko naso dojewa. Amma ganin yanda ya birkicemin a yanayin da bai taɓa ba bamma san na saki layi ba na zayyane masa komai. Tashin hankali na gani sosai a tattare da shi. Ya sake balbaleni da faɗa cikin ruɗani.         “Amma Samraah baki da hankali. Yanzu wannan abin na faruwa da ke tsahon sati biyu amma kika ja bakinki kikai shiru sai yanzune kike faɗa. Shima badan kunyi haka da Mansoor ɗin ba da bamu kamo bakin zaren ba. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un Samraah baki da wayo, wlhy sam baki da wayo. Dan tabbas bana raba ɗayan biyu mutumin nan ne yasa ake bibiyarki. Dolene ma ya gano kin ɗauki videon nan. Wannan abin shi nake gudu tun farko daman, shiyyasa kullum nake cikin tunanin mafita ashe nima nayi sakaci...”         “Yaya ban gane ba. Wai kana nufin wancan mutumin mai ɗaure gashi Maashi yake komi ma oho masa”.       “Idan bashi ba wanene Samraah. Tabbas dole shine zaisa a iya miki irin wannan bibiyar. Samraah kodai kinyi wani yunƙurine a kansa batare dana sani ba, dan na sanki da shegiyar wautar tsiya”.      “Wlhy Yaya ni babu abinda nayi, kaima kasan kuma bazanyi komai ba sai da saninka. Ka tambayi Mansoor ALLAH ne shaidata shima shaidatane. Daga office bana zuwa ko'ina sai gidan nan. Weekend kuwa islamiyya ce kawai ko Malam Umaru zai tabbatar maka da hakan shima. Toni wanema yunƙuri zanyi tunda kunce nabar komai a hannunku. Wlhy ko video ɗin tunda na adanashi ban sake waiwayarsa ba balle ma na kalla har wani yaji ko ya gani. Hatta da Mansoor ranar yake cemin ALLAH ya kiyaye yana rage abubuwa ya goge video ɗin nan, da ace banda shi a wayata da an samu matsala. Amma dan ALLAH na sake adanashi kada nayi sakaci tunda na sanshi shi da goge-goge a waya na tsiya.”            “Nasan baza'a samu matsala daga gareki ba Samraah. Amma dole mutumin nan yanada cctv camara ai, idan kuma mai yawan bibiyar abubuwane to tabbas anan ya gano shine yasa ake bibiyarki. Ko kuma wani ya ganki. Ina dai zuwa bari na kira Mansoor yazo ya same mu”.     Ban iya cewa da shi komai ba. Sai faɗawa duniyar tunani kawai da nayi. Harya kammala wayar bamma sani ba. Cigaba yay da kai kawonsa alamar haɗa lissafin abubuwa. Cikin abinda baifi mintuna talatin ba sai ga Mansoor yazo. Kasancewar lokacin sallar isha'i yayi suka tafi massalaci. Sai da aka idar suka dawo ina ɗakin Yaya ɗin dai har sannan. Mansoor na gaida daga haka suka shiga tattaunawa danni gaba ɗaya zuciyata bata tare da gangar jikina. Sai da Mansoor yaymin tambayar ni da waye muka je restroom ɗin a ranar? Dan tambayace da ya kamata ma ace sun min tun a waccan ranar amma basu yi ba. Saida na sauke ajiyar zuciyar dawowa hayyaci sannan na sanar musu ɗaya daga cikin securitys ɗin da suka bada tsaro a ranar ce. Na sake maimaita musu yanda mukayi. Sun sake tambayata bayan ita ban haɗu da kowa ba? Sannan itama ɗin sanda ta tafi yin wayar bata dawo bane nemana?.          “Eh gaskiya ni dai banga ta dawo ba, kasancewar ma hankalina ya tafi akan abinda ya faru ban sake bi takanta ba. Dan haka ban san miya hanata sake komawa ba. Kuma ni gaskiya bana jin nama sake ganinta har aka tashi”.        Kallon juna Yaya da Mansoor sukai. Cikin ƙarfin hali da nuna tashin hankali Yaya Musaddiq ya ce, “Anya kuwa security ɗin nan bata koma ba a lokacin. Idan lissafina yayi dai-dai, ta koma domin su fito tare kamar yanda ta mata alƙawari, maybe bata sameta ba ta shiga nemanta, ko kuma ta sameta a lokacin da take bude-buɗen ƙofar ko ma ɗaukar video ɗin. Dan inba haka ba babu yanda za'ai tai ɓatan dabo gareta. Hasashe na biyu lokacin da take faɗa maka ko wani ya jiku. Cikin biyun nan dole ɗaya ya tabbata, kuma duk inda zancen ya fito to tabbas an samu Maash an fargar da shi komai shiyyasa yasa ake bibiyarta.”        Cikin jinjina kai Mansoor ya ce, “Tabbas hasashen ka zai iya zama gaskiya Yaya. Amma ni a wannan gaɓar ma sai hankalina yaso rabuwa biyu akan wasu dalilai. Maash bawai ƙaramin mutum bane. Kana ganin ya aikata wannan kisan ya kuma san ya aikata har wata ace ta ɗaukesa a hoto mai motsi ya sani kuma ya zauna sakaci. Duk da yanda muke tunani abinda masu hannu da shuni ɗin nan suka tsana a rayuwarsu shine su binne wani laifinsu amma ya zama yana a hannun waninsu ko waninsu ya sani. Zakaga suna gaggawa wajen ganin sun daƙile komai. Idan lissafina yayi dai-dai wata fa kusan ɗaya kenan da faruwar komai. Kana ganin zai zaman ɓata lokacine akan wani bibiyar Samraah bayan yana da hanyoyi masu yawa dama zai karɓi video ɗin a hannunta batare da wata gargada ba. Karfa ka manta har hira yazo anyi da shi kuma itace tai da shi, randa aka saki hirar kuma ƙura ta tashi sosai da kace nace ɗin mutane harda masu cewa akwai alaƙa tsakaninta da shi, nasan dai kasan komai ba sai na sake maka bayani ba. Na kawo wannan hujjojin ne saboda bana son mu shagala da yawa a kan shine wanda kuma ke son ƙulla tsiyar na gefe. Kuyi haƙuri MD kansa na cikin zargina. Dan na jima da fahimtar yana son Samraah na hauka, randa kuma ta kai musu kayan saka bikin mu ya tabbatar ma da kowa hakan. Sai ƴar uwarku Baby. Tana sona matuƙa, wasu dalilai ne suke dakufeta, naji a majiya kai ƙarfi cewar tai alƙawarin sai tabi tako wace hanya domin ganin auren nan namu bai yiwu ba, dan tana da babban plan akan haka akwai kuma mai bata ƙwarin gwiwa ta bayan fage. Saboda yima kanta alwashin indai itama bazata sameni ba sai dai su rasa su duka. Da farko na ɗauki zancen shirme kawai irin nata na ƴan shaye-shaye, sai dai wannan abin na yanzu ya fara haskomin da gaske zata iya komai fa. Dan haka musa hankalinmu jikinmu domin tabbatar da ko wanene”         “Shaye-shaye kuma? Wai babyn ce ke shaye-shaye ko wa?” na faɗa ina kafe Mansoor da idanu. Murmushi kawai ya mun da faɗin, “Hum Samraah kenan, ke dai ALLAH ya shirya mana zuri'a kawai”.      Yaya na kalla a firgice, sai naga shi babu alamar mamakin zancen akan fuskarsa. Kasa haƙuri nayi sai da na ce, “Yaya kenan kaima kasan tana Shaye-shayen?”.     Sai da ya sauke numfashi mai nauyi sannan ya furta, “Na sani Samraah. Na kumayi iya yina na ganin ta daina amma hakan ya gagara. Na lurar da Abba amma ya nuna sharri nake mata. Tun daga nan na tattarasu na watsar”.       Zancen ya matuƙar girgizani gaskiya. Kamar yanda sosai maganar Mansoor tayi tasiri garemu ita game da MD da Baby da zasu iya sakawa a bibiyeni. Dan duk abinda ya faɗa gaskiya ne. Ni komai ma sai naji ya sake susuce min. Amma duk da haka Yaya yace bazamuyi sakaci da duka ɓangarorin uku ba. Zamu saka ido za kuma ku ɗauki matakin daya dace da kowanne. Dan haka zamu kai report wa yan sanda akan ana bibiyata, amma bazamuyi batun video ba fa, zamu bar ƴan sanda suyi aikinsu, idan ma Maash ɗinne da ga baya idan fito da videon ta kama sai muyi hakan. Nanma mun gamsu, kun kuma bashi goyen baya, duk da ni dai naso ace tun yanzu muka fidda video ma wa yan sanda. Amma ban san dalilinsu na son a ɓoye video ɗin nan kamar wani suna tsoronsa.       Kwana biyu dayin haka aka kawo lefena da ga gidan su Mansoor. Akwatina har goma sha biyu shaƙe da kayan alfarma na gani na faɗa. Babu wanda zaice lefen nan bai birgesa ba. Sai dai anga tsagwaron hassada daga Mom dan ta kasa haɗiye komai. Harda zage-zagenta wai ai saurayin Baby ne na kwace da asiri. Kuma ba kowa ke kawo min asirin ba sai Gwaggo Gudidi. Abu kamar wasa dai sai da aka kwashi rigima. Dan ƴaƴan Gwaggo Gudidi duk sun zo suna gidan. Rikici akai sosai na gaske. Lokacin Yaya Musaddiq shi baya gida. Yana wajen aiki, kamar dai wancan karon ya damƙa komai hannun matar ogansa aima baƙi abincin tarba da kayan maƙulashe. A wajen aikin ma ba zama yay ba shi da Mansoor suka fita police station wajen batun ƴan sanda. Sun shigar da report tare da bada lambobin mota har uku dana basu.. Suna can har aka gama rikin nan kowa ya kama gabansa dan su Gwaggo ma sun ɗauke lefen nawa daga gidan sun wuce da shi can gidanta. Acewarsu barinsa gidan Abba bazai yiwu ba su Mom zasu iya salwantarwa saboda basu da isashen mutunci. Ashe ko hasashen su Gwaggo yay dai-dai. Dan su Mom sun shirya mummunan ƙudiri kuwa akan lefen nan aka ɓata musu shiri. Wannan yasa suka huce kaina sanda na dawo. Dan bana gidan ma ni ina gidan wata ƙawata ta islamiyya. Duk yanda naso daurewa na kasa. Ranar sai da nai kuka sosai da jin kewar iyayenmu. Daga ƙarshe nai alwala nayi nafilfilina tare da miƙama UBANGIJI kukana. Wannan ɓacin ran dana kwana da shi yasa banyi aikin komaiba a gidan. Sai ma shiri da nai tunda farar safiya domin wucewa gidan su Joy ko zan rage damuwa, amma zan ɗan fara zuwa office saboda saƙon da MD ya turamin jiya da dare kusan 12 kan dan ALLAH yana son ganina a office yau idan babu damuwa. Jin yace abu mai muhimmanci ne yasa na amince zanje ɗin, kuma bana ma son yinin gidanmu a yau ɗin sam. Na fito na leƙa ɗakin Yaya sai na samu ya fita. Nayi mamakin fitar tasa ta sassafe yau. Amma sai nai wucewata akan zan kirashi awaya. Zuwa da rana sai na samesa a garejin dan ina son mu ɗan tattauna wani abu.          Napep na samu na shiga. Mun fara tafiya inata ƙoƙarin kiran numbern Yaya sai naji an kira sunana. Da mamaki na ɗago ina kallon wanda ke kusa da ni dana samu a napep ɗin, ganin babu wata alama data nuna shine yay kiran sunan nawa na kalla mai napep shima. Shima kuma babu alamar shi ɗin ne. Cikin takaici da jin haushi na sake ƙoƙarin maida kaina ina mamaki. Sai kuma aka sake faɗin, “Samraah!”. A fusace na ɗago yanzun kam. Kafin na samu damar cewa komai naji abu a fuskata. Yuuuu naji kaina ya fara mun. Cikin zabura nai yunƙurin dira daga napep ɗin sai dai na kasa hakan. Dan cikin ƙanƙanin lokaci jikina yay wani masifar nauyi na silale jikin kujera idanuna na lumshewa. Daga haka ban sake sanin mike faruwa ba kuma......✍️ _Duk da nasan Maash ya bada kwangilar bibiyar Samraah. Amma nima zancen Mansoor ya fara sakani a cikin ruɗani. Amma bana son ku ruɗe kumuje zuwa dai, dan har yanzu fa wasan ma bai fara ba. Yaya Maash ne da wannan aika-aikar ko kuwa MD? Zai iya zama Baby ma fa. Kai Mom ma ba barinta zamuyi ba. Shin waye yay kidnapping Sam-G🤥🤔?._ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_ ......Tunda suka tashi Mom taga Samraah batai aikin komai a gidan ba ta ƙara harzuƙa. Lallai yau dolene taci uban yarinyar nan dai-dai gwargwado har sai taga ubanda ya tsaya mata a gidan nan. Fuuu ta nufi ɗakin barcinsu tunda tasan yau weekend bata fita aiki. Sai dai me wayam babu Samraah. Sai auta da Bibaa dake barci. Da farko tai tunanin tana wanka. Dan haka ta koma falo tai zaman bala'i tana jira. Bayan kamar mintuna goma sai ga Bibaa ta fito tana miƙa da alama tashinta kenan.        “K koma ko kiramin yarinyar nan Samraah”.      Da ɗan mamaki Bibaa ta ce, “Ai bata ɗaki Mom.”     “K ban san iskanci ki duba toilet mana ina zata je”.    “ALLAH Mom bata toilet yanzu fa na shiga bayin na fito. Kodai tana kitchen tana aiki?”.              A ɗan ƙufule Mom ta ce, “Tunda ni makwauniya ce ko. Dalla fita nasan tana ɗakin shegen can shima munafukin na biyu. Jeki daga shi har ita ki kira min su”.      Babu musu Bibaa ta amsa da to. Sai dai babu jimawa sai gata ta dawo wai ɗakin a kulle yake. Dai-dai nan Abba ke fitowa da ga ɗakinsa. Tambayar mike faruwa yayi dan tun ɗazun yake joyo hargagin Mom da ga cikin ɗaki. Aiko a cikin tsantsar masifa take sanar masa. Ɗan jimm yay kamar ba zai ce komai ba. Sai kuma ya zaro wayarsa a aljihu ya shiga neman Yaya Musaddiq. Bugu biyu kuwa ya ɗauka. Daga can ya gaida Abban cikin girmamawa. A daƙile ya amsa masa kamar yanda ya saba. Kafin ya ɗora da faɗin, “Kai kuna ina ne?”.      Da mamaki Musaddiq ya ce, “Abba ina gareji. Akwai wanda zai zo ya ɗauka motarsa ne shiyyasa na fita da wuri”.           “Uhhmyim ita Samraahn tana tare da kai kenan?”.     “Samraah kuma Abba. Ni kam mi zaisa na taho da Samraah nan. Tana nan a gida ai na barta tunda yau bazata je aiki ba”.     A harzuƙe Abba ya ce, “To bata nan”.       Sosai zuciyar Musaddiq ta wani harba. Muryarsa na nuna alamar rawa ya ce, “Abba kamar ya bata nan. Ina Samraah zata je da sassafen nan bayan bata da office yau?”.     “Sai ka tambayen tunda yawo nake da ita a bayana”. Daga haka Abba ya yanke wayarsa. Hankalin Musaddiq yay masifar tashi batare da yasan dalili ba, tunda ta saba duk inda zata ko baya gida sai ta kiransa ta sanar masa a waya. Dan haka babu arziƙi ya baro gareji da fatan ya zo ya samu Samraah ta dawo. Dan tunda Abba ya katse wayarsa ya maida akalar kiran kan Samraahn amma wayar na shiga anƙi a ɗauka. Daga baya ma aka kasheta duka baki ɗaya. Wannan kuma ba halin Kandalarsa bane ba, balle ma ace shine yay kiranta da kansa...      Cikin ƙanƙanin lokaci ya iso gidan, inda ya samu har lokacin Mum nata masifarta. Al'amarin kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Dan kuwa dai har sha biyun rana babu wani bayanin Samraah. Tun kowa na ɗaukar komai wasa har la'asar babu wani bayani. Zuwa lokacin anata buge-bugen waya wa ƴan uwa amma kowa sai yace bata je ba. Hakama ƙawayenta duk da Musaddiq yasan ita bamai yawan biye-biyen gidajen ƙawaye bace, ƴan uwan ma wace ala cika. Har gidan su Mansoor an sani zuwa sannan. Zuwa kusan biyar na yamma sai ga ɗayar wayarta an samu, wanda ya ɗaga ya tabbatar musu tsinta yayi. Harga ALLAH kuma ya yarda zai basu ne saboda yaga hoton Samraah ne a fuskar wayar. Hankali tashe Mansoor da Musaddiq sukaje inda ya kwantata yake, dan su ne dai keta faɗi tashin. Su Mom sunce basu yarda wani abune ya sameta ba sai dai idan yawon tazubar ɗin data saba tafiya ne ta tafi. Dan haka sukai burus da komai kamar basu san mima ake ba. Garama Abba yakan yi ɗan zugumm alamar tunani. Da Mom ta tsikaresa da hira kuma sai ya ware.     Mansoor da Musaddiq sun amso waya tare da mask ɗin Samraah da eyeglasses ɗinta da aka tsinta. Ya kuma kaisu inda ya tsinta ɗin mutane kuma da yawa sun bada shedar tsintar yayi da gaske. Dan abun ya faru ne a idon mutane kusan uku dake sana'a a dai-dai wajen. Kasancewar suna fitowa da safe sosai suma. Sai dai sunce sunga wata napep da mota blue sun tsaya a wajen amma basu san mi sukayi ba, sai da suka wuce ne wanda ya tsinta wayar yake ganin abinda ya tsinta ɗin. Kuma yay magana da su bai ɓoye ba. Zuwa yanzu kam hankalinsu yakai ƙololiwar tashi, dan haka take suka kai report a station mafi kusa. Dalilin Mansoor nada ɗan halinsa tun a lokacin aka shiga traicing ɗayan layin Samraah. Dan kuwa wayoyinta biyu ne, kuma duk manya ne. Ɗaya tana amfani da ita saboda aiki, ɗaya kuma abinda ya shafi family ɗinta da ƴan abubuwanta ne a ciki. To ta aikin aka ajiye aka tafi da waccan. Har dare babu wani cikakken inpometion mai gamsarwa, zuwa sannan kuma dai tashin hankalin Abba ya fito fili. Dan Gwaggo Gudidi tazo tana faman kuka da faɗin lallai a binciki su Mom sun san inda suka ɓoye Samraah. Tunda kowa yaji dama abinda Mom ɗin ke faɗa a jiya gaban kowa. Mom zata hayayyaƙo maƙwafta da suka shishshigo suma suka nuna lallai akwai ƙamshin gaskiya a batun Gwaggo Gudidin. Kamar wasa kuwa sai ga rikici ya ɓarke. Dan zuwa gab da magrib su Musaddiq suka zo anguwar da ƴan sanda. Nanfa hankalin Mom yaso ya fara tashi, sai dai tana ta ƙoƙarin dannewa ita a dole kada aga gazawarta..        Tambayoyi ƴan sanda suka musu har Auta ba'a bari ba. Mum kamar a ruɗe take amsa komai, dan haka ɗan sandan da case ɗin ke hannunsa ya dasa mata ayar tambaya. Sai dai bai ce komai ba suka wuce akan zuwa safiya zasu iya dawowa kosu nemesu a can station ɗin su. 💫 (✧✧)✨(✧✧)✨(✧✧)💫 Sannu a hankali na motsa idanuna da sukai min matuƙar nauyi da ɗaurewa. Sai kuma na shiga buɗesu sannu-sannu, a wani ɗaki mai ƙarancin haske na tsinta kaina alamar yamma tayi. Dan kiraye-kirayen sallar magrib ma naketa jiyowa. Ƙirjina ne yay wata masifar bugawa. Nai saurin ambaton ALLAH ina sake lumshe idanuna da sake buɗewa. Tabbas ta tabbata anyi kidnapping ɗina. Da ƙyar na iya tashi kasancewar duk jikin nawa babu wani ƙarfi. Ga wani irin fitsari da nake ji. Jiri-jiri dake neman kwasata yasa da ƙyar na iya dafe bango na miƙe. Lalube na shigayi ko zan samu wani haske. Cikin ikon ALLAH na samu makunar fitila. Idanuna dake lumshewa da buɗewa na sake warewa da ƙyau. Ɗakine babba sosai. Sai katifa a ƙasa ƙarama irin ta ƴan makaranta, akwai bargo da filo an kuma shimfiɗa bedsheet a kanta. Gefe kuma handbag ɗina ce sai leda mai tambarin gidan abinci har guda biyu a kusa da ita. Tare da ledar ruwa guda. Da ƙyar na iya jan ƙafata zuwa ƙofa. Na shiga ƙoƙarin murɗawa amma sai na sameta rufe gam. Inda labule yake ma sake nufa da ƙyar dan nasan bazai wuce window ba, na turesu da ƙyar. Ita ɗince kuwa, sai dai a rufe, nai ƙoƙarin na buɗe da ƙyar. Amma ƙarfen da akai adonta da shi ƙanana ne sosai ta yanda ko hannu bazai fita ba ma. Sosai zuciyata ke rawa yanzun kam. Ban haƙuraba na sake nufar ɗayar, nan ɗin ma dai irinta ce. Inda ke da kamar ɗan corridor na nufa, amma sai na samu ƙofar bayi ce a wajen. Naga hakanne sakamakon buɗewa da nai. Bamma san sanda na silale a wajen ba na saki wani irin kuka mai tsuma rai da girgiza zuciya. Na jima zaune a wajen ina kuka kamar numfashina zai rabu da gangar jikina. Kafin na sake miƙewa da ƙyar na shiga toilet ɗin. Fes yake babu wani datti. An kuma ajiye wadataccen sabulun wanka, omo, toothpaste brush, sosan wanka. Kai harda kayan wanke bayi. Babu dai abinda zaka nema ka rasa daya shafi hakan. Alwala na ɗaura batare da nabi takansu ba, zuba ruwan alwalar a jikina ya ƙara taimakawa naji na ɗan warware. Anan ma sai da na duba window sai dai yayi sama sosai koma ƙarami ne. Haka na fito na dawo ɗakin. A saman tabarma dake gaban katifar malale nai sallar azhar da la'asar har magrib. Sake kife kaina nai a wajen na sake buɗe sabon shafin kuka. Nama rasa ina zan kai tunani na. Kamar wadda aka zaburar na zabura inda bag ɗina take. Da sauri na buɗeta na shiga laluben wayata jikina har wani mazari yake tsabar yanda nake a ruɗe. Ganin kamar laluben ma baya min kawai na zazzage komai na cikinta burina kawai wayata ya faɗo, amma babu ita babu alamarta, sai ƴan kayan shafana dana zuba lips gloss ne kuma da fauda sai ƙaramin oil misk da face mask guda biyu da bana rabo da ita a jaka akoda yaushe. Bamma san na sake sakin wani wahallen kuka ba a wajen tare da zubewa ƙasa daga ni har bag ɗin........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒘𝒐_ .......Kusan mintuna biyu ina zabga kuka, kafin na sake jawo jakar da tarkacen ciki dana juye ƙasa duka zuwa gabana. Sake zazzagawa na koma yi kamar wadda ta zautu. Ko abinda keda alaƙa da waya babu a cikin duka wayoyina biyu. Amma na kasa yarda, sai ƙara zazzagawa nake da ɗaɗɗaga kayan dana zazzage kamar wata mai neman barimar ɗan kunne. Sai da dai zuciyata ta tursasani akan babu ɗin da gaske sannan na sake fashewa da kuka tare da yin wurgi da jakar. Haka na kasance a wannan daren babu wata nutsuwa irin ta cikakken mai hankali a tare da ni. Sai dai koda wasa ban mance ambaton UBANGIJINA ba. Gab da asubahi wani wahalallen barci yay awon gaba dani, ban tashi farkawa ba sai kusan bakwai da kwata. A firgice na miƙe na nufi toilet na ɗauro alwala. Bayan nazo na gabatar da salla koda na idar a wajen na cigaba da zama na fara karatun Alkur'ani a hankali jikina duk babu ƙarfi, dan akwai yunwa ma tare dani, jiya gaba ɗaya banci ba ban sha ba. Nafi awa ɗaya da kusan rabi a wajen naji ana ƙoƙarin buɗe ƙofa. A zabure na ɗago daga cusa kaina da nai cikin ƙafafuna dan a haka nake karatun. Kallo ɗaya mai shigowar yamun ya ɗauke kansa, yana sanye da mask baƙi kamar yanda komai na jikinsa ke baƙi, dan hatta hannunsa akwai safar hannu baƙa. Ya kuma toshe idanunsa na baƙin eyeglasses da babu abinda zan iya ganewa ko gani nashi. Irin ledar dake ajiye a ɗakin ce a hannunsa. Batare da ya tankamin ba ya ajiye ya ɗauki ta jiya dako kallonta banyi ba ya nufi hanyar fita abinsa.       Muryata na rawa nai saurin dakatar dashi ta hanyar faɗin, “Wanene kai? Miyasa kuka kawoni nan? Mi kike buƙata da ga gareni? Wani laifi na muku ko kuɗin fansa kuke nema?”.      Duk da ya tsaya cak tun fara maganata bai juyo ba. Ina kammala faɗa kuma bai tanka ba ya buɗe ƙofar ya fice tare da sake kulleni ta baya. Ido kawai na zubama ƙofar wasu kalar hawaye na gangaro min da gudun tsiya. Lallai ina a tsaka mai wuya, gashi bamma san wanda zan iya zarga ba. Dan gaskiyar Mansoor ne. A wannan gaɓar hatta da Baby da MD kai har Mom da Abba kansa ni zasu iya shiga lissafina ma. To amma ni abinda ke damuna waɗan nan mutanen da duk na lissafo idan sunyi hakan gareni duk miye ribarsu? A yanzu ba kaina kawai nake tausayi ba  ƴan uwana da halin da zasu shigane ke matuƙar tada min hankali fiye da komai. Ga Mansoor shima. “Ya rabbi ina roƙonka da sunayenka ƙyawawa masu tsarki ka kuɓutar dani da gaggawa. Kasa kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya a zukatan ƴan uwana da masoyana da ni kaina. Duk wanda bashi da laifi akan wannan al'amarin ya ALLAH ka hanashi shiga wahala. Mai hannu a ciki UBANGIJINA ka hanashi damar cutar dani koda yayi niyyar hakan a gareni”. Zamewa nai a hankali na sake kwanciya ina mai cigaba da karatun Alqur'ani na. A haka barci ɓarawo yay awan gaba dani tunda dama bai isheni ba. Ga kaina na wani kalar masifaffen ciwo.       Barci nayi sosai, dan ban tashi farkawa ba sai da naji ƙarar an buɗe ƙofa. Firgigit na miƙe kuwa ina murza ido. Mutumin ɗazu ne dai kuma kamar ɗazun fuskar tasa a rufe. Wata ledar abincin ya sake ajiye min da wata babba fara ita kuma yanzu ma ya sake ficeewarsa batare da yamun magana ba ya sake kullenin. Kwata-kwata yanzu ma hawayen nawa sun kasa fitowa. Da alama zuciyar ta fara dakewa. Salloli da nake jiyowa anatayi a masallatai yasa na miƙe a hankali. Jikina sai ciwo yake tako ina. Na tabbatar harda rashin wanka dan ni mutum ce mai son yawan wanka a rayuwa. Kuma ko yaya idan banyi ba sai na dinga jin babu daɗi. Naso na daure kada nayi, kamar yanda nake ƙoƙarin hana kaina cin komai, dan ko ruwa sai a wajen alwala nake ɗan haɗiyarsa. Amma na kasa hakan dan wani ƙyanƙyamin kaina nama fara ji, harma zuciyata na wasi-wasi akan yin salla da su. Ledar kayan na janyo na shiga fiddosu. Dogayen riguna ne har biyar duk marasa nauyi da bazasu takurani ba. Sai hijjab biyu manya. Harda su b&p shidda-shidda. Sai kayan barci har uku da man shafawa da turare. (Ko wanene wannan anyi cikakken ɗan iska ma wlhy. Wato komai anyisa akan shirine, babu kuma alamar zan bar nan ɗin a kusa tunda harda tanadin kayan sakawa). Duk a zuciya nake wannan tunanin. Cikin jin ban aminta da ɗakin ba na ɗauka doguwar riga ɗaya da b&p na shiga toilet. Wanka nayi da ruwa masu ɗumi dan akwai hitter a toilet ɗin. Sai naji jikina ya rage nauyi, hakama zuciyata. Na ɗan ji ƙarfi da nutsuwa har ƙwaƙwalwa ta na iya sarrafa tunani yanda ya kamata. Brush shima nayi na ɗauro alwala na sake fitowa. Banbi takan mai da abinci ba na koma na kwanta a katifar na lumshe idanu kawai ina mai faɗawa duniyar tunani.....        ✨💞✨💞✨💞✨     Zuwa safiya labari ya fara karaɗe gari da social media. Abinka da sananniya musamman ma a watanni biyun nan da sunanta yay amsa kuwwa a lungu da saƙo sakamakon abinda ya faru a wajen taron buɗe Companyn Maash da kuma hirar da tai da shi. Ta wani ɓangaren kuma wanda basa harkar yanar gizo sun santa ne a dalilin shirin da take gabatarwa ta hanyar rediyo. Duk wani wanda ke a office ɗinsu hankalinsa a tashe yake. Musamman ma MD da ƴan sanda suka gano shine mutum na ƙarshe daya tura mata text message akan yana son ganinta. Dan haka a ranar Monday ɗin ƴan sandan suka gayyacesa office ɗin su. Gefe kuma gasu Mom suma an tattare zuwa station saboda abinda sukaita faɗa a randa aka kawo lefen Samraah, ga kuma rikicin da suka sake yi a daren bayan mutane sun watse maƙwafta da suka ji komai sun faɗa da sake tabbatar da anyi hakan. ALLAH sarki Mansoor da Musaddiq sai su baka tausayi. Dan kwana ɗaya kacal duk sun fita hayyacinsu. Hafizzullah ma a ranar Monday ɗin ya tsallako karatunsa ya nufo Kano..        Shigar mahaifin Mansoor a zancen ya saka ƴan sanda sake ɗaukarsa da girma. Dan a yanzu D.c.o ɗin ne ma da kansa yake gudanar da binciken. A yau har Attahir ma Yayan Mansoor ba'a bari a baya ba, dan shima dai yana a station ɗin anata ɗan kai kawo dai akan batun...    Al'amari kamar wasa akan ɓatan Samraah ƙaramar magana na neman zama babba. Dan ƴan sanda sun matuƙar takurama MD da Baby da Mansoor ya tabbatar da yana zargi. Sannan wani mai shago a anguwarsu ya tabbatar da yaga sanda Samraah ta tare napep ta shiga, dan har gaida shi ma tayi kamar yanda ta saba. Ya kuma tabbatar da zai iya gane napep ɗin dan har number ɗinta da tambarin dake jikinta ya riƙe saboda mai napep ɗin ya jima tsaye a ɗan nesa da shagonsa shi yama yi zaton ko wani yake jira a wajen. Sai can ya maida hankali ga sallamar mutane sai ga Samraah. Lokacin da take gaishesa tabbas ya ɗago ya kalleta yaga tana ƙoƙarin tsaida Napep. Sai dai bai ga mai shirin ɗaukar tata ba har sai da ta shiga ciki. Mai napep ɗin ma yaja sun fara tafiya, ya ɗan zabure da nufin tsaidasu dan hankalinsa yaji bai kwanta ba amma har sun wuce. Sai kawai ya bisu da addu'a tunda bawai yasan gaibu bane, kuma yaga bayan ita akwai wani kamar ma a ciki.        Bayanin mai shagon nan yayi matuƙar yima ƴan sanda da duk wani masoyin Samraah daɗi. Dan koba komai an fara kama bakin zaren. Sakamakon kamar yanda mai shagon nan ya faɗi tambarin dake jikin napep ɗin nan haka mutanen da aka ajiye wayarta a inda suke suma suka maimaita dan tambari bai kamata a manta da shi ba. Wannan yasa duk wani masoyinta buɗe idonsa tarwai akan lura da shigi da ficin masu napep duk da kuwa kamar banza suke a Kano dan yawa. A ta gefen jami'an tsaro kuwa kai tsaye ofishin shugaban masu kula da ƴan napep suka je. Inda suka bada report akan napep ɗin da mai tuƙata. A take kuma babu ɓata lokaci aka shiga bincikenta. Abinka da komai a tsare a yinin ranar sai da aka gane wanda ke tuƙa napep ɗin. Tuni ƴan sanda suka saka aka cikuykuyosa shi da napep ɗin tasa. Inda wanda suka gani suka tabbatar da ita ɗin ce kuwa. Sai dai basu da tabbacin shine a ciki ko ba shine ba. Amma tabbas dai napep itace.          Kasancewar dare yayi ba'a wani tuhumi mai napep ba a ranar sai washe gari da Samraah ke cika kwanaki uku kenan. Sai dai me, a yayin tuhumar mai napep yayi rantsuwa ya ƙara kan shi bai san komai ba. Hasalima a ranar napep ɗin ba'a wajensa ma ta kwana ba. Ya bama wani abokinsa da yamma akan zai yi aiki ya ɗan samu nashi har zuwa dare sai ya dawo masa da ita. To bai dawo masan da ita ba sai washe gari kusan takwas dan har sukai faɗa ma saboda ya karya masa alƙawari, ga shi shi kuma yana fita aikin wurine amma ranar yasa ya makara........✍️      _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_ ......D.c.o ya tura yaransa neman abokin mai napep, sai dai an samu wai baya nan yayi tafiya. Wannan dalilin yasa sukace zasu cigaba da riƙesa har sai an kamo abokin nasa. Hankalin ƴan uwansa ya tashi kamar yanda shima nashi ke a tashe. Amma dai d.c.o yaƙi saurarensu. Dan ya tabbatar musu da yana akan aikinsa ne. Babu yanda zasuyi dole suka haƙura suka tafi. A ɓangaren ƴan media suna nan suna cigaba da tattauna batun ɓatan Samraah. Yayinda hotunanta ke yawo lungu da saƙo kowa na faɗin abinda fahimtarsa ta bashi. Dan wasu har suna danganta komai da cewar ita ta jama kanta. Dama taya zata taɓa irinsu Maash tace zata zauna lafiya. Ai gashi nan ya mata lunbu-lunbu da ga ƙarshe ya ruftata dan mawuyacine ace bashine ya saka aka kwamusheta ba. Musamman in akai dubi da yanda ta samu damar tattaunawa da shi ta yanda manyan ƴan jarida suka daɗe suna fatan haka amma basu samu ba. Wasu ko na ganin wani ne ya saceta dan kawai a ƙullama Maash sharri. Wasu na ganin ko dai MD ɗin nasu ne musamman yanda zancen son da yake mata ya karaɗe ko'ina, ga shi kuma an saka mata ranar aure da ya rage saura sati uku kacal. Wasu dai kuma zarginsu na akan Maash ɗinne dai da tunanin son da yake mata ne ya sashi aikata hakan ganin an saka mata ranar aure da waninsa. Hakama wasu zarginsu bai bar kan Baby ba itama jin TAKUN SAƘAR dake tsakaninta da Samraah ɗin akan Mansoor ba, hakama mahaifiyarta da tun fil azal ba son su Samraah ɗin take ba. Ga kuma abinda tayi a randa aka kai lefe. Kai hatta da abokan huɗɗar Mansoor ɗin wasu a ciki sun shigo zargin jama'a. Tawani fannin kuma akance maƙiyane kawai ko kidnappers ne kawai saboda yanda sunan Samraah ɗin ya samu ɗaukaka cikin ƙanƙanin lokaci game da shirin da take akan matasa da yanda take nuna illar lalacewar matasa a cikin al'umma. Kaso marasa ƙarfi kuwa na ganin adai bunciki sauran samarin Samraah suma dan zasu iya aikata komai ganin Mansoor na shirin wuff da ita, ko kuma shi ƴammatan Mansoor ɗin. Kai zance ne dai gashi nan kala da iri harda wanda ma bashi da ma'ana. Kamar wasa a haka sati ɗaya ta shuɗe ana fakon abokin mai napep. Ba'a samu damar damƙosa ba kuwa sai a randa take cika kwanaki tara ciff.     ★ “Kidnapping kuma? Ni wlhy yallaɓai bani bane. Mizai sa nai kidnapping mutum? Idan na ɗauketa ma ina zan kaita?”.      Cikin tsawa yaron d.c.o dake tuhumar tasa ya ce, “Kai karka raina mana hankali. In ba kai bane ba to waye bayan abokinka ya tabbatar da kai ya bama key ɗin napep ɗin tasa? Kuma da ita aka ɗauketa daga nan ba'a sake jin labarinta ba har yanzu”.      “Tabbas ni ya bamawa yallaɓai. Kuma ba ranar muka fara yin haka da shi ba. Saboda nima lokacin da nake da napep ɗin nakan bashi. Hasalima nine na koya masa tuƙinta, da taimakona kuma aka bashi napep ɗin ma a office ɗin mu. Amma wlhy ni banyi kidnapping kowa ba”.      “Ƙarya kake yi kai ne. Tunda har ka iya barin gari sai yau kake dawowa a tunaninka komai ya lafa ko”.    “Ranka ya daɗe ni ban bar gari dan komai ba wlhy. Ƙauyenmu naje da yake ina noma duk shekara. Shine na je nakai taki gonata. Can ɗin babu network shiyyasa wlhy bamma san mike faruwa ba. Sai yanzu da nake ji ma a bakinka. Amma na tuna wani abu, idan ban manta ba da safe abokinmu da shima mukanyi irin haka da shi yazo yace na ara masa key ɗin keken Salisu zai amso saƙo a tasha, tasa na gareji sai azhar zai amso.”      Da sauri ɗan sandan ya ce, “Ka tabbata?”.        “Tabbas anyi haka ranka ya daɗe. Dan ƙanina ma na ɗakin a gabansa akai komai. Yaje kusan awa biyu sai gashi ya dawo ya kawomin yay godiya. Har ma naji haushi saboda ya saɓa lokacin daya dace ace na maidawa Salisu kasancewar yana fitar sassafe shi”.       “Yanzu ina zamu samesa?”.   “Anguwarmu ɗaya da shi, sai dai ta bayan layinmu gidansu yake. Shima kuma yana harkar adaidaitan, nasan yanzu baza'a iya samunsa a gida ba sai irin takwas haka ko bayan magriba gaskiya”.             “Karka damu zamu samoshi”.      Ɗan sandan ya faɗa yana miƙewa. Kai tsaye office ɗin d.c.o ya nufa. Bayanin da yaron ya masa duk ya maimaita masa. Goyon baya d.c.o ya bashi akan su tabbatar sun samo wancan yaron kafin zuwa safiya. Ya tabbatar masa da in sha ALLAHU za'ai hakan kafin ya bashi damar fita. Cikin girmamawa yay salute ɗinsa sannan ya fice. Shiru kawai d.c.o yay yana mamakin wannan irin juya-juya. Dan case ɗin gaba ɗaya ya ɗauki zafi saboda yanda mutane keta ka-ce-na-ce akan batun yarinyar, shi kansa yanda yaga an ɗauki al'amarin nata da muhimmanci ya sashi bibiyar shirye-shiryenta na baya a daren jiya, tare da shafukanta na sada zumunta dake ɗauke da fallowers masu yawan gaske, sai yaji ta shiga ransa. Gata dai ƴar yarinya amma akwai kaifin basira da nuna kwazo akan aikinta. Ga mahaifin Mansoor da Mansoor ɗin sun addabama rayuwarsu. Kowane motsinsu yanzu yana a station ɗinsu ne. Azalzalar su kawai suke faman yi akan a gano musu inda Samraah ɗinsu take su dai. Hakama Yaya Musaddiq idan ka kallesa sai ya baka tausayi, rashin dauriya kawai Mansoor ya fisa. Shiko Hafizzullah sai dai kuka. Yayinda jikin Abba ya fara sanyi, sai dai yaƙi yarda ya nuna hakan ga mutane saboda shakkar Mom.. ⭐❤️⭐❤️⭐❤️⭐❤️⭐ Faɗa muku yanayin da nake ciki a kwanaki tara ɗin nan da suka gabata sam bazai yiwu ba. Dan koda da kwatance nace zanyi hakan bai zama lallai ku iya fahimtata yanda ya kamata ba. Abinda kawai nake so ku fahimta al'amarin sam bashi da sauƙi. Nayi kuka matuƙa Bily. Irin wanda ni kaina sai da na tabbatar da nayi sa. Sai dai ku sani badan kaina nake yinsa ba. Domin ƴan uwana biyu ne da nasan zasu fi kowa shiga tashin hankali ne. Sai kuma masoyina da ya rage saura kwanaki goma sha uku kacal ya amsa sunan mijina. Dai-dai da daƙiƙa ɗaya ban gaza wajen miƙama UBANGIJI kukana akan ya kuɓutar dani daga wannan ƙangi, ya sa ina da rabon komawa ga dangina. Bani da wani ƙarfin nuna yunƙurina saboda halin rashin lafiya da nake ciki. Ciwon kai da zazzaɓi sun kasa barina. Na kuma gagara faɗama wanda ke zaryar ajiyemin abincina da har yanzu bai taɓa min magana ba, ban kuma taɓa ganin fuskarsa ba. Sai a yau da safe kusan goma da rabi sai gashi ya shigo. Nayi mamakin shigowar tasa saboda ba lokacin kawo min abinci bane, kuma baya shigowa dama sai zai kawo abincin. Amma ganin waya a kunnesa yasa na zuba masa manyan idanuna. Har gabana ya ƙaraso, batare da yamun magana ba ya tsaya ƙiƙam a kaina kamar wani mai gadin gidan kallon kwallo. Wayar dake a kunnensa ya sauke. Batare da yamun magana ba ya ajiyeta a ƙasa gabana. Na ɗago da nufin kallonsa maganar da akai cikin wayar ta katseni. Da sauri na maida kallona akan wayar, wata dattijuwar murya ce da nake ji kamar na taɓa saninta, cikin nuna ƙarfin iko da tabbatar da rashin wasa aka furta. “Nasan zuwa yanzu kin fahimci inda kike ba wajen wasan yara bane ba. Ba kuma filin ɗaukar rahoto bane ko dandalin sada zumunta. Baƙya buƙatar wani bayani kam dogo yanzu ƴammata. Sanin wanene ni? Miye dalili? Mi kika aikata duk bana buƙatar ji. Video recording ɗin hannunki kawai nake buƙata, mi zanyi da shi, ko minene alaƙata da shi ba damuwarki bane. Na duba a duk wayoyinki babu kin ciresa a ciki, ya rage naki faɗar inda yake ko wajen wanda yake a bani ke kuma ki kama gabanki. Idan kuma kikace zaki zama mai taurin kai tabbas zaki dawwama a wannan ɗakin tamkar kabarinki, dan ko mutuwa kikai a ciki zamu gina miki kabari mu bizne ki batare da wani mahaluki ya taɓa sanin hakan ba har abada. Kuma zan mallaki video ɗin sannan na ɓatar da duk wani ahalinki daga doron ƙasa. Zaɓi ya rage naki lokaci na tafiya miki dan nasan kina shirin zama amarya”. Ni kaina ban san sanda murmushi ya suɓuce min ba. A karan farko na wani ja numfashi mai nauyi tare da sakin wata siririyar dariyar ƙarfin hali. Kaina tsaye na nima na furta,........✍️ _Shin wa kuke tunani ne? Gashi dai Sam-G tace muryar Dattijo, kai nafa ruɗe nima. Amma mu haɗu a comment section ko wani zai canko mana🤔😞_ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒇𝒐𝒖𝒓_ ........“Oh oh wannan irin dogon zance haka Baba, bakinka ko gajiya bayayi. Kayi haƙuri ina jin girman tsufarka a cikin raina duk da ba ganinka nake ba. Sai dai ga saƙo zan baka. Ka faɗama shi wanda ta aikokan shin tsoron Samraah Abdul-wahab Gwarzo yake ne? Ko kuwa shi bai cika namiji bane daya laɓe a bayan tsufarka a yimin barazana? To idan yana kusa da kai ya buɗe kunnuwansa da ƙyau ya saurareni, idan kuma baya kusa ka masa recording. Ni Samraah Abdul-wahab Gwarzo ban yi video ɗin dan aimun barazana na bada ba. Idan buƙatarsa yake mu haɗu gaban hukuma. Idan kuma yana da ƙarfi yazo muyi gaba-da-gabq kwanta. Sai dai ya sani ko dungurin wani da ga cikin ahalina yayi bazai sauke hannunsa ba video ɗin zai baza duniya. Dan haka zaɓi ya rage nashi, ku farka daga wannan nannauyan barcin na barku lafiya”. Da ga haka na yanke wayar tun kafin shi ya yanke. A fusace wanda ya kawo min wayar yake hararata. Amma nai biris da shi na ɗauke kaina. Kiran wayar aka sake yi, da sauri ya ɗauka ya kai kunne. Ban san mi aka faɗa masa ba na ga dai ya sake hararata ya juya ya fita. Nima da harar na raka nasa bayan ina taɓe baki. Da ga haka na zame na kwanta zuciyata na wata irin tafasa. Sai dai a wani gefen ina jin daɗi dan koba komai na samu bakin zaren wanda yasa aka kawoni nan. Zargin mutane da yawa ya fitamun a dai zuwa yanzun, musamman ma jama'ar gidanmu.         Barcina na sha yau da rana sosai, dan yanzu bani da wani aiki sai inci in kwanta ɗin, sai idan naji na gaji ne da zaman waje ɗayan sosai nakan ta zagaye ɗakin wani lokacin ma na ɗan motsa jikina dai, saboda na fahimci na fara ƴar ƙiba ba kamar sanda aka kawoni da bana cin abinci ba sai yawan kuka. Ganin zan halaka kaina a banza nama masoyana asara yasa na fara cin abincin tunda nasan ban isa canja abinda yazo a littafin ƘADDARA ba ai. A yanayin ɗan ƙarfin jiki dana tashi da shi ya sani jin zan iya tunkaresa koda zai ƙarar da numfashi na, sai dai zan fara da wannan mai kawo min abincin a yau ɗin nan. Amma sai zuciyata ke gargaɗina da hakan kai tsaye, dan haka na shiryama raina wata sabuwar dabara ina kuma addu'ar cin nasarar hakan amma sai na gwada plan ɗin farko baiyi ba tukunna dai.      Kamar ko yaushe cikin ƙarfin hali na tashi nai wanka da ruwan ɗumi. Kaya na saka na sake dawowa na kwanta a katifar dan jiri nake ji na neman ɗibata. Ina nan kwance tamkar mai barci naji ana ƙoƙarin buɗe ƙofar. Luff na sake kwantawa har aka shigo aka sake maida ƙofar aka kulle. Sai da ya shigo tsakkiyar ɗakin sannan ya tsaya cak. Idanu na ɗan ƙara buɗewa ta can ƙasa yanda zan gansa da ƙyau. Ƙofar bayi yake kallo, nasan kuma dalilin yin hakan, dan kan shower ɗin na ɓalle nabar ruwa nata zuba. Ka ɗan naga ya duƙa yana kai yatsansa biyu ƙasa ya dangwala, sai kuma naga yay saurin ajiye ledar abincin hannunsa ya nufi toilet ɗin da alama ruwan ne ya fara fitowa.        “Lafiya miya faru?”.   Na faɗa a hankali. Bai tanka min ba, bai kuma tsaya ba. Na saki murmushi ina tashi zaune. Bayansa na bi. Duƙe na samesa yana ƙoƙarin buɗe hanyar da ruwa ke fita gaba ɗaya da ɗayan hannunsa. Ɗayan kuma ya danne pipe ɗin shower ɗin ya cusa babban yatsarsa a ciki ya tsayar da ruwan. Sai dai duk da haka yana ɗan fita sii. Da wannan damar nai amfani nima na shigo ina faɗin, “Tun ɗazu nake kiranka dan ka duba amma baka amsamin ba.”      Kaɗan ya juyo ya kalleni sai kuma ya sake maida kansa ga abinda yake yi. Ni ko na duƙa kamar zan janye masa boket dana jiƙa kaya ciki na samu nasarar zare wayarsa. Da sauri na tusata cikin rigata. Na janye bokatin na fita abina. Sake komawa nai cikin katifar nai kwanciyata. Sai dai zuciyata sai faman gudu take a ƙirjina. ALLAH ALLAH nake ya zo ya fita kafin ya farga babu wayar tasa. Amma bai fiton ba sai kusan bayan minti goma. Batare daya kallan ba ya nufi hanyar fita. Cikin rawar jiki ina jin ya kulleni ta baya alamar ya tafi kenan. Na ciro wayar. Naji daɗin ganin babu password jiki, cikin rawar jiki data hannau na saka number Yaya Musaddiq na danna masa kira. Harta katse bai ɗauka ba. Hankalina ya sake tashi jikina har kakkarwa yake. Sake ƙoƙarin kira nake ina kallon ƙofar. Nan ma ta shiga amma har tana neman yankewa babu alamar za'a ɗauka. Nama gama sadaƙarwa dan idanuna har sun cika da hawaye sai ya ɗaga. A yanda yay sallama cikin wani yanayi na mutum mai damuwa yasa idanuna sun ciko da ƙwalla. Cikin rawar muryar alamar son sakin kuka na ce, “Yaya Musaddiq nice. Nice kandalarka. Dan ALLAH kuzo ku fiddani anan karna mutu. Yaya banda lafiya ciwo zai kasheni. Sun kawoni nan sun ɓoye kullum sai dai suyita bani abinci kawa.....”     Fittt naji an ƙwace wayar daga hannuna. Hannu ya ɗaga zai ɗauke fuskata da mari sai kuma miya tuna oho masa ya tsaya cak. Niko tsoron da naji na kar ya kai ƙaton hannunsa kaina ya sani dunƙilewa waje ɗaya na rumtse ido. Jin shiru banji saukar marin ba na buɗe idona. Dai-dai nan yake ƙoƙarin fita a ɗakin. Na taso kuwa da uban gudu na nufi ƙofar nima, ina gab da ƙarasawa ya datse da sauri. Zubewa nai a wajen na saki wani kalar kuka mai ban tausayi da cin zuciyar mai sauraro.. Ina a wajen ko cikakken minti biyu baiyi da fita ba sai gashi ya dawo cikin sassarfa. Jin saukar handkerchief kawai nai a saman face ɗina. Kamar waccan ranar nayi niyyar yunƙurin tashi amma abinda suka shaƙa min yaci ƙarfina. Kamar ƙyaftawar ido na sulale ƙasa, daga haka ban sake sanin abinda ke faruwa ba kuma.. ✨●●)(●●)(●●)(●●✨       Gaba ɗaya yanda Yaya Musaddiq da Mansoor suka rikice bama su fahimci wayar ya yanke ba. Dan suna tare ne a mota sanda Samraah ta kira wayar. Da farko hankalin Mansoor ba'a kan Musaddiq yake ba. Sai da yaga yayi wata shegiyar zabura yana ƙwala kiran sunan Samraah jikinsa har wani gab-gab yake na rawa sannan. Wayar shima ya fisga jikinsa na rawa yake faman kiran ta. Sake ƙarɓewa shima Yaya Musaddiq ɗin yayi. Duk sun rikice sun ruɗe, jin dai ɗif ɗin yayi yawa suka ɗan fara dawowa hankalinsu. Sai sannan suka fahimci wayarma ta yanke. Wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga rige-rigen sakkoma Yaya Musaddiq. Dan harga ALLAH yana matuƙar ƙaunar ƙanwarsa. Mansoor ma dai idonsa cike yake da ƙwalla, cikin ƙarfin hali ya buɗe motar ya fita. A ɗan zabure Musaddiq ya figi wayarsa dai-dai sanda Mansoor ke fita a motar, dan tunawa da ya dace ma su kira d.c.o fa. Kiran nasa kuwa yayi, sai dai ba'a ɗagaba. Cikin tashi hankali ya cigaba da kira. Har 3 miscall, fita yay da sauri a mota. A jikin motar ya samu Mansoor jingine idonsa a lumshe. Cikin sauri-sauri yake faɗin, “Na kira d.c.o amma bai ɗagaba. Inaga ya kamata mu ƙarasa police station ɗin mu sanar masa”. Shima ɗan zaburar Mansoor yay, cikin alamar gamsuwa da zaburowa ya nufi motar yana faɗin, “Hakane yaya, wlhy ni kaina ma ya tushe na rasa mizan yi, amma bara na kira Yaya Attahir ya nemesa tunda abokinsa ne”.      Musaddiq ya gamsu da hakan, cikin ƙanƙanin lokaci Mansoor ya sanarma yayansa halin da ake ciki, kafin suma su ɗauki hanyar zuwa police station ɗin. Sosai Mansoor ke gudu, hakan yasa cikin ƙanƙanin lokaci suka iso station ɗin. Sun samu d.c.o baya nan ya fita sai dai Yaya Attahir ya kira Mansoor ya sanar masa yay magana da d.c.o ɗin ta waya, gashi nan zuwa ma su jirashi. Dole sukai zaman jiran dawowarsa duk a ƙage. Sai bayan kusan mintina sha biyar kuwa sai gashi ya dawo. Ganin yanda suke hankali a tashe ya buƙaci fara ganinsu. Suna gaya masa kamar yanda Attahir ya sanar masa tun a waya, shiyyasa ma ya katse abinda yake acan ya taho, ya amshi wayar Musaddiq tare da kiran yaronsa yace ya kwashe number ɗin yanzun nan ai masa tracing. Amsa yaron nasa yay ya kwashe number ɗin ya fita da hanzarinsa.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒇𝒊𝒗𝒆_ ......A matuƙar hanzarce cikin tashin hankali yake bin umarnin ogan nasa. Ita daya shaƙama abu ya fara kinkima ya kai mota. Ya sake dawowa ya tattara duk abinda ya shafeta ya fita da su suma. Hatta kayan data jiƙa domin wankewa bai bari ba. Bedsheet da komai ya tattare katifa kawai ya bari a ɗakin. Cikin abinda bai wuce minti goma ba ya bar gidan da ita da komai nata. Cikin uban gudu ya nufi hanyar inda ogan nasa ya sashi maidata. Yayi nisa a tafiyarsa saƙo ya shigo masa. Sanin wayar da mutum ɗaya take da alaƙa ya sashi taka birki da sauri ya ɗan gangara gefen hanya. Titine da bai cika yawan kai kawon motoci ba saboda sabuwar anguwace sosai kuma a gefen gari ne ma. Idanu ya waro matuƙa sakamakon ganin saƙon da ogan nasa ya turo masa, tare da sauri ɓalle murfin wayar kasancewar ƙarama ce dama ya cire batteryn shima ya zare layin. Karyashi yay huɗu yay cilli da shi yana mai kwanciya akan steering ɗin da sauke nannauyar ajiyar zuciya mai ƙarfi. Yayi kusa minti biyu a haka sannan ya ɗago. Samraah dake kwance a baya tamkar gunkiya ya kalla, cikin cije baki ya ɗauke kansa. Motar yay ƙoƙarin sake tadawa akai knocking glass. Da wani irin bala'in sauri ya kalla gefen nasa, dan motar tinted glass ne da ita shiyyasa. Yasan wanda yake ta wajen bai ganinsa, amma shi yana ganinsa. Ganin kamar babu wani alamun kasancewar sa jami'in tsaro ya sashi sauke gilashin a hankali. Matashin saurayi da bai wuce sa'ansa ba ya ɗan sake duƙowa da faɗin, “Barka oga. Badai wata matsala bace ba ko?”.         Murmushi yay shima cikin sauri ya ce, “Barkanmu. A'a babu komai na ɗan tsaya amsa kiran waya ne kawai. Nama gama yanzu zan wuce”.     “A to masha ALLAH, dama ina tunanin ko akwai matsala ne. ALLAH ya tsare hanya”.      Godiya ya masa yana ƙoƙarin maida gilashin kawai yaga an buɗe murfin gefensa an shigo. Da sauri ya juyo nan ɗin. Mutum ne garjejen gaske gashi cikin baƙaƙen kaya kamar shi. Sai dai wannan yasan ko'a mafarki sukai wasan kokawa ɗagashi zai dingayi yana nanawa da ƙasa. Amma cikin dauriya ya ce, “Malam lafiya kuwa?”.       “Itace ta kawo haka”.    Mutumin ya faɗa a gadarance. Sai kuma ya sa hannu ya zare key ɗin motar yana faɗin, “Fita ka koma baya”.     “Na koma baya kamar ya? Ni da motata ka shigo min babu wani neman excuse kace kuma na fita na koma baya. To kai a wa kuma?”.     Uffan mutumin baice da shi ba. Sai ma ɗora masa bindigar daya zaro a jikinsa yay a saman cikinsa. Da sauri saurayin ya kalla bindigar, cikin son ɓoye tashin hankalinsa amma yana ta son bayyana kansa ya ce, “Malam miye kuma na bindiga anan?”.     Shi dai bai tanka masa ba. Sai ma ƙoƙarin saƙala yatsarsa yake akan kunamar bindiga ɗin, shima sai kawai ya buɗe motar ya fita zuciyarsa na wata irin bugawa da sauri. Turus yayi jikinsa na tsuma ganin zuƙa-zuƙan motoci har biyu baƙaƙe wulik, ga Samraah ana ƙoƙarin sakawa a ɗaya. Sai garadan maza har uku irin wanda ya titsiyesa a mota tsaitsaye da bindigu suma. Yana ji yana gani haka ya shiga bayan motar dan dolensa, saboda babu makami ko ɗaya a tare da shi. Kodama akwai ai sarkin yawa yafi sarkin ƙarfi. Sannan waɗan nan kam sunfi ƙarfinsa, dan yama riga ya sadaƙar kawai jami'an tsaro ne su ɗin.         Shima abu suka shaƙa masa, a take ya sulale sai barci. Daga haka bai sake sanin a wace duniya yake ba sai farkawa yay ya gansa a inda bai taɓa sani ba. Dan ɗaki guda shima aka ajiyesa shi kaɗai. A yanzu kam hankalinsa ya fara tashi ƙololuwa. Dan ya fahimci ba ƴan sanda bane ba. To ko ogan nasa ne yasa akai masa haka? Amma mizaisa yay hakan kuma?. (Ka nema ɓata masa aiki mana) wani ɓangare na zuciyarsa ya ayyana masa. Kansa ya dafe da ƙyar, dan gaba ɗaya jikinsa yay masa nauyi. Jin kamar jiri na ɗibarsa ya ɗan zame ya sake kwanciya yana mai lumshe idanunsa...       (✿(✿(✿)(✿)✿)✿)      A ɓangaren su Yaya Musaddiq kam anyi traicing number da Samraah tai kiransa an kuma gano inda suke. A take babu ɓata lokaci d.c.o ya shirya mutanensa. Duk yanda yaso su Mansoor su zauna sun dage da roƙon son binsu, ya fahimci koda ya hanasu zasu iya binsu a baya, hakan kuma akwai haɗari dan haka ya haƙura aka fita har dasu. Sunyi tafiya baifi ta mintuna uku ba layin ya yanke. Da sauri yaron d.c.o ya sanar masa.        “Oga akwai matsala fa. Da alama sun farga damu dan layin ya daina aiki. Hakan na nufin an ciresa a wayane, dan da yana kan wayar ko kasheta sukai zamu same su”.     Shima hankalin d.c.o ya tashi, amma sai ya dake shi cikin bada umarni ya ce, “Ku ƙarasa har inda layin ya dakata da aiki”.        “Okay sir”.   Ya faɗa yana yanke wayar. Su Mansoor basu san halin da ake ciki ba. Dan suna a ɗayar motar ne. Gashi kuma an cigaba da tafiya kamar yanda aka faro. Cikin abinda bai gaza mintuna talatin da biyu ba suka iso dai-dai wajen, dan gefen gari ne sosai. Sun sami mota kaɗai, amma babu alamar mutum. A take duk suka fito, sauran da basu san mike faruwa ba duk sun zagaye mota da bindiga. Wanda dai yake kamar ogan tafiyar ne ya sake kiran d.c.o ya sanar masa cewar gafa mota sun samu, sai dai basu sani ba koda mutum a ciki ko babu. Nan ma umarnin bincikawa ya basu, dan haka suka fara aikinsu, sai dai an hana Mansoor da Musaddiq zuwa kusa da motar duk da yanda suke a zalame.       Cikin kulawa da ƙwarewar aiki aka buɗe motar, sai dai me babu kowa a ciki sai kayan Samraah harda jiƙaƙƙun nan na botiki, sun cigaba da bincike motar tako ina, har suka samu nasarar ganin layin wayar a gefen titin an karyasa. Wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga kwaranyoma Musaddiq, hakama Mansoor ya duƙar da kansa jikin motar ƴan sandan kawai da alama shima dai kukan yake yi. Dan ba sai an faɗa musu ba komai ya tabbatar musu da mutanen nan sun sake samun nasarar tserewa da Samraah kuma.      Komai an tattara har motar aka wuce da su station. Wasu a cikin ƴan sandan kuma suka watsu a wajen ta cikin jejin har ma da cikin ƙauye dake ata wajen bisa umarnin d.c.o. Dan yana zargin wanda suka ɗauke tan ko dai sun shiga jejin, ko kuma sun shiga cikin ƙauyen domin tsira tunda har aka samu motarsu anan. Sauran ƴan sandan da suka wuce station nata ƙoƙarin kwantarma da su Musaddiq hankali. Dan a take sun nema bayanai daga companyn layin wayar da Samraah tai kiran Musaddiq. Za'a binciki dukan abinda akai da layin a kwanakin da suka gabata. Kai tunma daga randa aka sayesa. D.c.o ya tabbatar musu da in sha ALLAHU za'a dace tanan. Badan dai sun gamsu ba suka haƙura suka tafi, dan bayanan sai zuwa gobe za'a samesu... (✿(✿(✿)✿)✿) Tunda na farka daga nannauyan barcin dana kasa tuna lokacin farawarsa rufin ɗakin da nake kwance kawai nake iya kallo. Rufine dake tabbatar da ba'a ƙaramin gida nake ba. Dan yanayinsa da fentin bangon ɗakin kawai ya isa ya tabbatar da haka. Na jima a hakan kafin na motsa da ƙyar. Saman gado nake, tabbas hakan ne, na ayyana a raina cikin tabbatarwa da kaina. Komawa nai na sake kwantawa batare dana ƙarasa tashin ba. A take komai ya shiga dawo min dalla-dalla. Na zare wayar wanda ke gadina na kira Yaya Musaddiq, bayan ya ƙwace ya shaƙa min abu, daga haka ban sake sanin komai ba. Kenan dai ɗakkoni yay daga can gidan ya maidoni nan saboda gudun tonan asirinsa. Hakan na nufin babu rana balle watan komawa ga zuri'ata. A hankali wasu hawaye suka shiga silalo min masu zafi. Yau saura kwanaki takwas aurena, na tabbata duk hankalin wani masoyina ba'a kwance yake ba zuwa yanzu. Musamman Yaya Musaddiq, Mansoor, Hafizzullah... Wani murɗawa da marata tai ya katse min dukan tunani na. Faɗuwa gabana yay,  Dan kuwa lallai lokacin prioud ɗina ne. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Aiko akwai matsala, idan na kasance a wannan halin anan waye zai kula dani? Dan ba ƙaramar wahala nake sha ba har sai an mun allura, wani lokacin ma ai allurar taƙi sauka. Shiyyasa har shan magani nake a ɓoye dan kar jinin yazo. Abinka daba uwa ba balle ta gani ta kwaɓa, sai babu wanda yasan ina hakan har yanzu, kuma na jima inayin hakan, dan ko yanzu kusan watana na biyar kenan banyi ba saboda bana wasa da maganin a duk sanda nasan kwanakin period ɗina sun gabato, yanzu ma da ace akwai shan kawai zanyi shike nan bazai zo ɗin ba. Jin yaɗan lafa min na sake buɗe idanuna tare da yunƙurawa da ƙyar na tashi zaune. Ɗakine babba, sai dai babu komai a cikinsa sai iya katifar da nake kai, ashe ba gado bane, irin ƙatuwar katifar nan ce irin wadda ba'a sakawa a gado. A hankali na miƙe da ƙyar, windows ɗin ɗakin nabi na lalleƙa, sai dai bana iya gane komai sai dai ina iya jiyo magana mutane ƙasa-ƙasa. Hakan yasa na nufi inda nake ƙyautata zaton ƙoface. Bugawa na shigayi babu ji babu gani ina kuka. Sosai nake ma ƙofar bugun hauka da nasan dolene ya damesu. Amma ƴan iskan nan kamar kurame, ga wani irin murɗi da marata kemun na azaba, tun ina ƙarfin hali har na sulale ƙasa jikin ƙofar na zube. Tuni nayi sharkaf da zufa na azaba, ga jikina dake rawa, sai kuma uban kuka da nake ina kiran sunan ALLAH da fatan Yaya Musaddiq ya zo ya ɗaukan.........✍️      _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒔𝒊𝒙_ .......Dukkanin bayanan da d.c.o ya buƙata an kawo daga companyn layin wayar mutumin. Dan haka yay zaman dubawa daki-daki. Sabon layi ne, an kuma buɗesa wata ɗaya daya gabata. Sai dai ba'a taɓa waya da kowa da shi ba sai number Yaya Musaddiq da Samraah ta kira. Sai kuma number ɗaya jal da sakwanni kawai aka dinga tura masa da ita. Dukannin sakwanin kuma a gajarce ne. Babu kuma wata ma'anar da za'a fahimcesu sai su da suka yi abinsu. A yanda kuma sakwannin suke kamar babu sanayya tsakanin wanda ke amfani da layin da mai tura saƙon da alamu suka tabbatar shine ya saka akai kidnapping Samraah ɗin. Abin ya tsayama d.c.o a zuciya. Amma dai ya sake bada number da ake tura saƙon itama a basu bayani a kanta. Nan ma sunce sai washe gari. Hakan yasa d.c.o sakawa ai masa traicing number ɗin kafin su kawo bayananta. Sai dai me sam layin babu shi akan network kwata-kwata ma. Hakan na nufin shima mai shi ya karya shi ɗin kenan ko ya yarda ko ya sauke. Wani irin dukan ɓacin rai d.c.o ya kaima desk ɗinsa. Dan ya fahimci wannan al'amari gaba ɗaya akwai rainin wayo a cikinsa. Duk kuma wanda ya shirya ɗauke yarinyar nan yana da basira ƙwarai da gaske. Dan bai ɗauketan ba sai da ya gama tsara dukkan hanyoyin ɓullewarsa daki-daki ta yanda gano wanene shi zai yi matuƙar wahala. Amma babu komai, ai dole ne ko yaya yayi kuskure. Da kuma wannan ɗan ƙaramin kuskuren kaɗai zasu iya kama shi in sha ALLAH..        Ranar da kansa ya zo gidan Abba ba yaransa ba. Lokacin kuma anyi sa'a duk suna gida. Hatta Nabil yazo weekend bai koma ba dan shi a hostel yake zama. Hafizzullah dai ya koma bisa tirsasawar Yaya Musaddiq. Da farko kicin-kicin Mum tai da fuska. Dan ita fa magana ta gaskiya zancen Samraah ɗin nan ya fara isarta. Zirga-zirgan da ƴan sanda ke musu kullum a gida yanzu ta fara cimata rai. D.c.o dake ta binta da kallo cikin dakewa ya ce, “Ina ganin muna gab da ganin Samraah in sha ALLAHU”.      Mum data gama cika taf cikin ɓacin rai ta ce, “Yo dama kune ke wahalar da kanku, duk ma inda take ai itace takai kanta. Dan ni nasan abokan iskancinta tabi wani garin kawai suke zaman shashancinsu a wani wajen. Amma yallaɓai duk kunbi kun tadama kanku hankali muma kun gagara barinmu mu huta. Haba, Samraah dai Samraah dai kamar wata allura ko sarƙar gwal ko diamond”.            “To amma Hajiya duk kin san da haka miyyasa baki sanar mana ba tun farko?”.      “Ni! Rufamin asiri na mutu maza su kaini ba mata ba. Taya zan sanar muku kuwa yallaɓai. Ace kuma na laƙa mata sheri. Kadai san ɗan riƙo komi zaka masa ba tsira kake ba. Amma tun yaushe wannan yarinyar ke bin maza suna barin gari. Wane hotel ne bata san da zamansa a garin nan da wajen garin ba. Ai ni bana raba ɗayan biyu wannan yarinyar ta zubar da ciki sama da sau bakwai kuwa. Tunda nan zata dinga mana ihu da murƙususu wai mararta na ciwo, haka zakaga jini na binta, in ba zubda ciki ba kuwa mi tayi?”.       Kai kawai d.c.o ke faman jinjina wa. Yayinda Abba keta hararar Mum da mata alamar tai shiru amma matar nan sai da takai aya ta haɗiyi yawu bakinta kamar an ɓarka zani.  Kallon Abba d.c.o yayi bayan ya gama ɗan rubuce-rubucen sa. “Amma Alhaji matsayinka na uba duk kasan da hakan baka taɓa ɗaukar wani mataki ba?”      Kafin Abba yay magana caraf Mum ta sake amshewa. “Matakin mi zai iya ɗauka a kanta yallaɓai. Bayan duk gidan nan babu wanda take shakka ko tsoro tafi ƙarfinmu. Sannan ɗan uwanta duk da saninsa take komai tunda shine kawalinta.....”      “Amma Hajiya ina magana da mijinki ne. Shi kuma nake son ya amsa min wannan tambayar.” kai Mum ta ɗauke gefe tana laɓe baki. D.c.o ya sake maida hankalinsa ga Abba da yanayinsa ya nuna sam baya jin daɗin abinda Mum ɗin keyi, amma ya gagara tsawatar mata. “Kai nake saurare Alhaji”.      “To yallaɓai ni mizance. Al'amarin ne gaba ɗaya akwai ruɗarwa. Amma ina yin iya bakin ƙoƙarina, sai dai kasan mu maza koda yaushe kana waje ba zaman gidan kake ba, shiyyasa ita ta fini sanin abubuwan”.    Shiru kawai d.c.o yay tare da zubama Abba dake ta ƴan kame-kame ido. Yaya Musaddiq da idanunsa suka cika da ƙwalla cikin sarƙewar murya ya ce, “Ranka ya daɗe Samraah bata taɓa aikata fasiƙanci ba. Sannan inba akan aikin nan nata ba zan iya rantse maka bata taɓa shiga hotel ba. Sannan ciwo da takeyi tana yinsa ne duk wata sakamakon al'adarsu ta mata. Amma inaga abar maganar nan, duk kuma inda take in sha ALLAHU addu'armu na biye da ita. ALLAH ya bayyanata, ya kuma bata kariya daga sharrin duk wani mai sharri”.       Maganganun Yaya Musaddiq sun sake saka Abba shiga wani yanayi, dan sai zufa yake kamar wanda ya haɗiyi kunama. Yayinda Mum keta ƙunƙuni ƙasa-ƙasa tana jin kamar ta rufe Musaddiq da duka. Sai dai babu damar hakan kodan d.c.o dake zaune. D.c.o ya gamsu da zancen Musaddiq, dan haka bai sake cewa komai ba ya miƙe. Miƙewar shima Musaddiq ɗin yayi batare da ya sake kallon inda su Abba suke ba ma, dan bai taɓa jin ɓacin rai mai tsanani akan abinda suke musu ba irin yau. Wani irin zafi yake ji a zuciyarsa game da su matuƙa.... ★💫★💫★💫★💫★💫 Ciwo ne sosai yaci ƙarfina. Harma nake ganin ya ninka wanda nakeyi a baya. Ko hakan nada nasaba da yanda nasha magani wata na biyar kenan ma banyi ba. Sama-sama nake jin ana buɗe ƙofar. Daga haka ma nai ɗiff alamar hankalina ya gushe daga gangar jikina.        Da sauri wanda ya shigo ɗin ya koma baya ganin Samraah ta suma. Cikin tashin hakanli yake sanarma sauran ƴan uwansa, “Kai yarinyar nan fa kamar ta mutu”.     “Mutuwa fa?”. Suka faɗa a tare suma cikin zaburowa. Komawa yay da gudu yana faɗin, “Kuzo to ku gani wlhy”. Duk binsa sukai cikin sassarfa suma. Wanda ke da ɗan yanayin hausawa a cikinsu ne ya ce, “Kamar suma tayi dai, Ayo ka kira oga Please, kasan dai irin gargaɗi da sharuɗɗan daya gindaya mana. Kar muce zamuyi shiru mu samu matsa”.          “Exertly maganarka gaskiya ne.” ya faɗa yana ƙoƙarin danna waya. Duk cikin harshen nasara suke maganar. Baifi mintuna biyu ba sai gashi ya dawo. Ya sanar musu oga yace duk su fita a ɗakin za'azo da doctor yanzu. Hakan kuwa akai duk suka fita, Ayo ya kulle ɗakin kamar yanda aka umarcesa. Bako a cika minti talatin cif ba sai ga driver ya kawo doctor. Ita kaɗai ta shiga ɗakin bayan Ayo ya buɗe mata. Sai da ta ƙarema fuskar Samraah kallo kafin ta kira Ayo ya taimaka mata suka maidata saman katifar. Duk taimakon daya dace tai ƙoƙarin bata, cikin ko ƙanƙanin lokaci ta farfaɗo. Sai dai tana buɗe ido ta dafe mararta da hannu bibbiyu tana kuka da murƙususu sosai. Da ƙyar ma take iya amsa tambayoyin doctor ɗin. Kasancewar likitar ƙwararriya ba'a wani ja da nisa ba ta fahimci matsalar Samraah. A take tai kiran wanda ya sakata aikin. Ta sanar masa zata turo sunayen magungunan da alluran da take buƙata yanzun nan a sayo a kawo mata. Yace okay ba damuwa ta tura. Rubutawa tai ta tura, sannan ta cigaba da bama Samraah taimakon daya dace kafin a kawo. Ba'a ɗauki lokaci ba Ayo yay knocking, izinin shigowa ta bashi. Ya shigo ɗauke da leda yace an kawone a bata. Amsa tai da godiya, shi kuma ya juya ya fita.          Duk zafin ciwo baya hanani shiga ruɗani a duk sanda za'amin allura. Yanzun ma hakane. Dan tunda na fahimci abinda take shirin mun na birkice mata. Duk yanda taso tankwarani kuwa ta kasa. Dan da gasken gaske na tsani allura harma da magani. Dole tai kiran wani wai yazo ya riƙeni. Nako tubure akan wlhy babu shegen gardin da zai taɓani. Ta ɗauka azabar ciwoce kawai ta sakani faɗin hakan. Sai da mutumin data kira ya shigo yana kawo hannu sukaga na rarumi handbag ɗinta zan kai masa duka sannan. Shiko yay baya da sauri yana yare da ɗaga hannaye sama. Ina kallonta tai murmushi da bashi umarnin fita. Ita kuma ta ɗauki waya, sai da ta daddana sannan takai kunne. Ina jinta sama-sama tana sanarma wanda ta kira cewar ina tsoron allura, na kuma ƙi yarda a riƙeni. Ban san mi aka gaya mata daga can ba na dai jita tana cewa okay. Daga haka ma ciwo yaci ƙarfina har tai allurar bamma sani ba saboda yanda marata kemin azaba har ina shiɗewa. Sai gani nai kawai ta haɗa kayan tafiya. Babu jimawa barci ya ɗaukeni, dama haka allurar kemin duk sanda akayita.       In dai aka min irin allurar nan cikin amincin ALLAH da nayi barci na farka shike nan. Amma abin mamaki yau saɓanin haka. Dan cikin dare na farka amma da sabon ciwon mara da yafi na farko ma. Ciwo sosai harna suma sau kusan biyu. Bamma san yaya akai ba naga doctor ɗin ɗazun a kaina. Tare da wata fuska dana taɓa sani sai dai na mance a ina nasan fuskar dan ciwo ya sakani galabaita dishi-dishi nake ɗan ganinsu, amma tabbas nasan fuskar wannan mutumin, kuma ya kamata na tuna ina ne na sanshi.......✍️        _🥱Ya kamata ki tuno dai kam, koma fita a ruɗani muma Samraatu🚴._ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_ .......Yanzun ma dai barci ne mai nauyi sosai ya sake yin awon gaba dani batare dana gama tantance fuskar mutumin ba. Ban kuma farka ba sai washe gari da rana gatse-gatse. A yanzun ma dai ba farkawar daɗin rai bace ba. Dan still dai ciwon ne ya farkar dani ta yanda har sai da doctor ta sake dawowa. Yanzun kam naga alamun ruɗanin yanayin nawa a fuskarta itama. Dan bayan ta ɗan duddubani fita tayi tana danna waya, da alama magana take son yi da wani...        Bata wani jima sosai ba ta sake dawowa. Allurar dai ta sake fakar idona tamun, sai dai da alama tamafi ta jiya ƙarfi. Dan ko minti biyu cikakku banyi ba na sake komawa barci, daga haka ban san wainar da ake toyawa ba kuma...      A ɓangaren Doctor bayan tama Samraah allurar barci ya ɗauketa babu jimawa wanda tai kira a waya ya iso. Kamar yanda ta shawarcesa da kai Samraah asibiti ya amince. Sai dai da kansa ya nuna zai kaisu asibitin data tabbatar masa akwai dukkan tsaron da suke buƙata. Dan ya sanar mata alaƙarsu da yarinyar ta yanda hankalinta zai ɗauka bawai ainahin gaskiyar sato ta ko kwatota ne ma oho musu ba. Ita kuma jin wanda ya saka aikin yasa bata wani damu ko ɗarsa zargi a ranta ba take bata duk wannan kulawar. Dan tun jiya da tasan yana a garin Abujar nan take jin wani farin ciki, tasan kuma a dalilin aikin yarinyar nan zata iya haɗuwa da shi, duk da dai yanayin ciwon yarinyar yana buƙatar aje da ita asibitin da gasken..         Sun isa asibiti batare da wata matsala ba. An kuma yima Samraah dukkan binciken daya dace. Dan har dare suna a asibitin, sai kusan goma suka gano matsalarta. A take suka haɗo duk abinda zai taimaka mata a matakin farko kafin ai mata abinda ya dace. Gidan suka sake maidota aka saka mata drip kamar yanda ya buƙata, daga haka suka fice aka barta da masu tsaronta.      Tunda suka shigo katafaren ginannen gidan take jin jina kai da sakin kurmushi. Duk da tasan wannan ba komai bane daga mamallakin gidan. Amma dai tayi mamakin yanda yaron nasa ya bata labarin an ginashi cikin ƙanƙanin lokaci tare da wani ma a Kano. Duk da kuwa tasan yana da gidaje sosai a Abujar nan da basu da adadi ma musamman ga ita da ba kowanne ta sani ba, amma tasan wannan ɗin na musamman ne gaskiya. Har kusan ƙofar falon ya kai kafin yay parking, cikin murmushi yay mata nuni da suje ciki. Babu musu ta ɓalle murfin motar ta fita, sai wani taku take cikin yauƙi da yanga. Tun a takun farko na shigowa falon wani sanyi da ƙamshi mai sauke gajiya suka ratsata. Ta wani shaƙi iska da dogon hancinta ta fesar a slowly. Ko makaho yasan falon ya haɗu tamkar mai shi. A hankali ta ɗan kai dubanta ta gefen damarta da take jin ƙamshinsa yafi yawaita a tanan. Shine kuwa zaune cikin kujera 1sitter da laptop a saman ƙafafunsa daya miƙe saman Centre table. Yanda keyboard ɗin laptop ɗin ke bada sautin ƙara zai tabbatar maka da typing abu yake. Da alama kuma mai matuƙar muhimmanci ne. Dan gaba ɗaya hankalinsa na kan screen ɗin, kuma yana dannawa ne da ɗan yanayin sauri na ƙwarewar sabo da hakan. Ƙananun kaya ne a jikinsa kamar ko yaushe. Dan sune suturar da yafi sakawa sai ko suit kamar dangin yahudu. Sai dai kasancewar wandon nasa kaɗan ya zarta gwiwa ya bama ƙafafunsa damar bayyana samɓal. Har suka kai zaune bai kallesu ba balle ya nuna yasan da shigowarsu. Sai da ya ɓata kusan mintuna shida curr sannan yay magana batare da ya kallesun ba yanzu ma.          “Any problems?”.      Ya faɗa a daƙile cikin silent voice ɗinsa. Hayatu ne ya jin jina kai yana mai sake sakama kansa nutsu da gyara tsaiwarsa cikin nuna girmamawa sosai. “Eh to Sir dama dai akan batun yarinyar can ne. Kasan tun jiya na sanar maka abinda ke faruwa na rashin lafiyar da take ciki, har kace Dr Rumaisa tazo ta dubata. To tun dai jiyan tayi duk abinda ya dace amma ba'a dace ba. Ɗazun dai dole tasa mukaje da ita asibiti domin a bincika matsalar ta shine dama muka zo sanar maka dan yan zun ne muke dawo wa...”           Shiru kamar bazai tanka ba, sai da ya mula dan kasa ya furta, “Uhum ina sauraren ku”.     Da sauri Doctor Rumaisa tai tsigil ta ce, “Ranka ya daɗe Good evening”.       Bai amsa mata ba, illa ɗan jinjina kansa da yay kawai alamar amsawar kenan batare da ya kalleta ba kuma. Taji ba daɗi, dan ba haka taso ba. Amma sai ta daure ko za'a dace ta cigaba da faɗin, “Gaskiya yarinyar akwai babbar matsala a tare da ita. Da alama tun kafin yanzu tana fama da pain a duk sanda zatayi prioud, kuma yana mata tsanani. Maybe hakan ne ya jata ta dinga shan maganin hana zuwan prioud ɗin a duk sanda lokacinsa yayi, shine ya haifar da matsalar wannan karon ɗin. Dan sai wahala kawai take sha amma jinin yaƙi ya fita, yanzu dai in sha ALLAHU na mata dukkan abinda ya dace akoda yaushe zai iya fita ɗin, sai kuma ta kiyaye cigaba da shan wancan magungunan inba haka ba zatama kanta illa. Dan a yanzu hakan ma sai an ɗorata akan magunguna masu ƙarfi sosai da zai dai-daita mata komai, sai dai sunada wahalar samu maganin dan sunada tsada gaskiya, ba kowanne pharmacy zaka iya ganinsu anan ba ma”.       A yanzu ɗin ma dai babu alamar zai amsa dan kamar ma bashi takema bayanin ba. Hakan yasa Hayatu bata amsar dan yasan Maash bazai sake magana ba kuma. “Sir zan ƙarasa komai in sha ALLAH. Dama dai na kawota ne kawai ta maka bayani yanda zakafi fahimta.” daga haka yayma Dr Rumaisa nunin ta miƙe shima yana tashi. Sam ba haka taso ba, dan fuskarta ma ta nuna. Ta kafe Maash da kallo tana mai fatan ya sake cewa wani abu koda bazai ɗago ɗin ya kalleta ba, dan dama ita ta matsama Hayatu akan ya kawota ta masa bayani da kanta. Amma sai bai ko kallonsu ba aikinsa ma ya cigaba dayi kamar yanda suka shigo suka samesa. Sai ka ɗauka ma ya manta da su a falon ne tsabar halin yarfin mutumin nan.      Suna fita ta kalli Hayatu rai ɓace. “Amma ba haka mukai da kai ba Hayatu?”.        “To yaya kike so nayi doctor. Kin san dai halin Boss ba sai na sake tisa miki ba. Ba yau ne kika fara masa aiki ba kuma. Shiyyasa naso ma ki bari muyi komai mu gama iya mu kaɗai tunda ba gagara zai yi ba. Tunda kuma shine yasa kizo zai buƙaci ku haɗu kafin mubar garin. Yanzu dai kiyi haƙuri a madadinsa. Kiyi kuma magana da pharmacy ɗin da kikace zasu turo maganungunan nata. Sannan ki bada account number da za'a saka kuɗin.”         Gaba ɗaya fuskarta ta sauya da tsantsar damuwa da ɓacin rai. Duk da dai tasan zata shaƙi kuɗi a aikin nan, dan ko Hayatu hannunsa a buɗe yake tamkar boss ɗin nashi a wajen ƙyautatawa. Kamar zatayi magana sai kuma dai ta shanye da ƙyar, gaba tai idanunta na cika da hawaye ta buɗe motar da suka zo ta shiga. Murmushi Hayatu dake binta da kallo yayi, acan ƙasan ransa kuma yana jin tausayinta. Dan yasan tamkar ta ɗebo ruwan dafa kanta ne dakon soyayyar wanda soyayyar uwa kawai da familynsa ya sani sama data wata ɗiya mace a wannan rayuwar. Shi kansa har mamaki yake anya ogan nasa nada lafiya kuwa, dan shi dai zai iya rantsewa, bayan abokan huɗɗa dana aiki be taɓa ganin wata mace a gefen ogansa ba da sunan yana mata kallon mace mahaɗin rayuwa ko wani ɓangaren jin daɗin duniya. Shi dai kawai neman kuɗi, ina zaka business ina ka fito business. Abinda kawai ke birgesa da shi neman kuɗi bai taɓa shagaltar da shi bautan ALLAH ba. Ga shi dai nan da zubin tsagerun mutane, amma batun ibada babu wasa.. Motar ya shiga shima, yay mata key suka fice a gidan bayan securitys dake gate ɗin sun buɗe masa. Lallashi da daɗaɗan kalamai ya dinga gayama Doctor Rumaisa, acewarsa ta cigaba da addu'a, idan ALLAH ya ƙaddara Maash mijinta ne sai ya aureta. A hankali ta saki murmushi kan ƙyaƙyƙyawar fuskarta, shi ko ya girgiza kansa dan shima ya san dai gangan yake faɗa, dan ga wata can ma a Lagos data fita wayewa da komai ana tirƙa-tirƙa bayan na bayan fage da iyayensu suke faman masa tallarsu wasu ko sune da kansu suke masa tallar kansun. Shifa yasha ganin ballagazayen wasu matan na kuka akan Maash ko kwanciya yay dasu idana bazai aurensu ba, amma ko kallonsu bayayi ma balle su samu karɓuwa. Gaskiya kuɗi a mafi yawan lokuta fitinarsu tafi alkairinsu yawa. Shi shaida ne. Dan shi kansa ma da bashi ke da dukiyar ba yana cin azaba balle shi Maash ɗin da kansa. Aure ma da ƙyar akai masa a shekarar data wuce, yanzu haka matar nada ciki, amma kullum cikin faɗa suke akan rashin lokacinsa. inaga kuma matar mai gayya mai aiki da ake fatan ta shigo, ai duk wadda zata zauna da shi a matsayin aure kam sai ta jajirce, ko dai ta dinga binsa duk inda zai je itama taji a jikinta dan yawon ma ba hutu bane, ko kuma ta cigaba da hakuri da abinda ta gani kawai.......✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_ ......Har gidansu dake anan Abujar Hayatu ya maida doctor. Koda ya dawo a inda suka barsa nan ya sake samunsa. Yanda yaga fuskarsa tai kicin-kicin sosai ya sashi sake nutsuwa, kamar yaron da yayma mamarsa laifi kafin ya tafi makaranta. Sun kai tsahon minti uku a hakan yana satar kallonsa, shiko yana aikinsa kamar bai san da shigowar tasa ba. Sai can a bazata cikin daƙilalliyar muryar nan tasa dake fita silent ya furta, “Bani black tea”.       Da sauri Hayatu ya amsa da, “Okay Sir” yana nufar hanyar kitchen. Bai wani jima sosai ba sai gashi da abinda yace masan. Lokacin da yake amsa ya ɗan kallesa, hakan yasa Hayatu saurin rissinar da idanunsa, dan ko motsi ogan nasa yayi yasan abinda yake nufi. Shayinsa ya kai baki ya ɗan kurɓa sau biyu sannan ya sake kallon Hayatun. “Minace maka akan yarinyar nan?”.             “Sir wlhy ba laifina bane. Kasan tanada shegen naci, nunawa tai ma idan ban kawota inda kake ba a jiya da ciwon yarinyar ya motsa bazata taɓata ba”.        “Sai akace ita kaɗaice likita kuma?”.    “Am sorry Sir. Anyi kuskure amma za'a kiyaye in sha ALLAHU”.    Shiru kamar bazai sake tanka masa ba. Har sai da ya gama shan shayin ya ajiye kofin yana miƙewa sannan ya furta, “A dawo da yarinyar nan gidan”.            Wani mugun waro idanu Hayatu yayi yana binsa da kallo. Sai dai shi bai ko waiwayo ba har ya gama haye stairs ɗin da zai kaika inda bedroom ɗin sa ya ke. Jagwab Hayatu ya zube a kujera tare da faɗin, “Boss rigimarka tafi ta sojojin yaƙin basasa wlhy. Kai komai idan zuciyarka ta raya maka sai kace ayi baka tuna abinda zai iya zuwa ya dawo. Yarinyar da ake nema ruwa a jallo kawota gidan nan ai haɗari ne, mun ɗakkota da ga Kano jiya ALLAH ya somu mun fito lafiya, yau kuma kace a kawota nan. Mu kuma da muka zo jiya zamu iya wucewa akoda yaushe ya za'ai da ita a gidan nan da ko ƴan aiki duk maza ne?” ya zabga tagumi bayan ya gama sambatunsa babu mai bashi amsa. Sai dai yasan ko giyar wake ya sha bai isa ƙin bin umarnin nan ba kuma. Dole ya miƙe ya tattare kayan daya baza falon ya koma tsaf. Shima ficewar yayi domin duba ɗakin daya dace a saka yarinyar idan sun ɗakkota..... 💞💥💞💥💞💥💞     A hankali nake buɗe idanuna da sukai min matuƙar nauyi. Hakama jikina jinsa nake tamkar ba nawa ba dan yayi min jingim. Ga laima ina jina kwance a ciki kamar wadda tai fitsarin kwance. Hannuna na ɗaga da ƙyar nakai inda nake jin laimar na taɓo, da ƙyar na ƙara ɗago hannun domin ganin minene. Duk da dama shi ɗin nai zaton gani sai da gabana ya faɗi, nai wani kalar rumtse ido da ƙarfin gaske ina cije lips ɗina shima da ƙarfi kamar zan huda su. A dai-dai nan naji ana taɓa ƙofar, sake faɗuwa gabana yay, nai ƙoƙarin yunƙurawa dan na tashi zaune amma har an riga an buɗe. Rashin ƙarfin jiki yasa na kasa jawo blanket ɗin dake a gefe, duk da ma wani sashe na zuciyata mamakin ganin kuma a inda nake ya kamani. Dan nan ɗakine mai ɗauke da kayan gado complete, sannan yafi wancan ƙyau fiye da zaton mai zato ma gashi ƙato sosai.           Mutumin nan da sukai min allura tare da doctor a daren jiya ne ya fara shigowa. Sangamemen ƙato biye da shi da da ledoji a hannu. Muna haɗa ido da shi na kauda kaina. Shima nasa kan ya kauda, batare da ya sake kallona ba ya furta, “Waɗan nan naki ne zaki iya amfani da su. Bayan su duk ma abinda zaki iya buƙata akwaisa a ɗakin. Likitarki ta gama aikinta, har magungunanki gasu anan ta kawo”. Daga haka ya juya ya fita. Da kallo na bisa zuciyata na wani irin kai-kawo. Kenan dai da gaske mutanen nan ne sukai kidnapping ɗina. Sune kuma suka saka ake bibiyata? Hakan na nufin sun san na ɗauki wannan video recording ɗin dai kamar yanda nai tunani?. (Ya ALLAH ta yaya hakan ta kasance?) Na faɗa a zuciyata, a zahiri kam ina mai runtse idanuna dake cike da nauyi har yanzu. Na kai tsahon mintuna goma ina faman tunani kafin na yunƙura na tashi da ƙyar, dan dama yanayin da jikina ke ciki yasa bance da shi komai ba da ya shigo. Yanda na jiƙa wajen da jini ya bani tsoro sosai, kamar wadda tai ɓarin ciki jama'a, haka dai na daure na sakko, sai dai ganin an saka min abune a inda na kwanta ɗin ba ainahin gadon na ɓata ba na ɗan saki ajiyar zuciya. Abin mai kama da leda-leda katifa-katifa na tattare na ɗauke. Cikin ɗingisa ƙafata dake ciwo na nufi hanyar da nake ƙyautata zaton toilet ne. Shi ɗinne kuwa, sai dai ya tsaru matuƙa, dan da za'a bani zaɓin wajen kwanciya maybe na kawo katifata nan na shimfiɗa, bawai dan yafi ko ina ƙyau ba, kawai dai ya birgeni ne shima. Duk da rashin ƙarfin da nake ji haka nai ƙarfin halin gyara jikina yanda ya kamata, nai wanka da ruwa mai zafi sosai. Sai a lokacin kuma hankalina ke neman tashi tuna bani da pant balle azo ga batun bad, sai dai tuna abinda yace yasa na fito. Ledojin da suka ajiye na shiga buɗewa, ta farko abinci ne, ta biyu kuwa kayan ciye-ciye ne. Sai ta ƙarshe ce ke ɗauke da kayan sawa, a ciki na samu pants da bad ɗin. Duk da naji wani iri da ganin hakan banda damar ƙorafi, ɗauka nai kawai na koma ciki na kimtsa jikina na dawo ɗakin. Kayan na sake buɗewa na ɗauki doguwar riga na saka batare da na damu da sanin sauran abinda ke ciki ba. Bana jin yunwa, dan in har ina a wannan yanayin ban cika son cin abinci ba, sai masifaffen kwaɗayi kamar sabuwar mayya. Dan hankalina duk yana akan naman can dana gani, ko naso basarwa kuma bazan iya hakan ba, garama naci bai nak yanda zan samu ƙarfin sauke musu abinda ke kaina. Zama nai kuwa nacisa sosai har saida naji na ƙoshi, na fiddo magungunan dana gani na duba duk yanda aka tsara shansu suma nasha.        A yanzu bana buƙatar zaman yin dogon tunani, tunda na fahimci a hannun waɗanda nake saɓanin kwanakin da suka gabata da nake canki canka da rashin tabbas. Yanzu babbar damuwata ahalina. Na tabbata duk inda Yaya Musaddiq da Mansoor suke hankalinsu a matuƙar tashe yake kodan kiran da nai a waya. Amma ina fatan askine yazo gaban goshi, dan nayi alwashin komi mutanen nan zasumin bazan taɓa basu video ɗin nan ba ko faɗa musu a inda zasu samesa, iyaka dai suce nima zasu halaka ni, ban damu ba, dan hakan da zasu yi shine mafi girman kuskure da zai tona asirinsu insha ALLAHU.         Shan maganin ya ƙara saka min jin daɗin jikina. Sai dai damuwa data kasa ɓoyuwa a kan fuskata. Sai gajiyar zama waje ɗaya daban saba ba. Nida nake yini tsaye kan ƙafafuna ina faman bautar aiki, garama idan office naje akan ɗan samu sassauci tunda shi kusan daga zaune ne. Motsin sake buɗe ƙofa da naji ya sakani tashi daga kwancen da nake cikin kujerar ɗakin, ɗan kwalin abayar naja na rufe kaina zuwa ƙirjina da ƙyau. Dai-dai nan aka ƙarasa shigowa. Mutumin ɗazu ɗinne dai, daga bakin ƙofa ya tsaya yayinda ni kuma nake kallonsa a tsiwace. Dan sai yanzu ne komai ke dawo min game da sanin da nai masa. Tabbas shine yaron mutumin nan mai kama da ƴan daudu ko nace ɗan daba ma ko sara suka oho duk ya cancanta, shine kuma ya kira da PA ɗinsa a ranar wancan taron. Nai saurin kauda kaina ina ƙoƙarin dai-daita fuskata da jikina. Tsahon mintuna kusan biyu ɗakin shiru, kafin cikin son nuna jarumta na furta,          “Dama kune kukai kidnapping ɗina?”.       Maimakon bani amsar dana buƙata sai jinai cikin bada umarni ya ce, “Zaku iya shigowa”. Baima ko gama rufe baki ba kuwa garadan samari biyu suka shigo. Ko namiji yaga wannan samudawan dole ya ji tsoro balle ni, amma dai nayi ƙoƙarin dake zuciyata ban bari tsorona ya fito a saman fuska ba. Sai dai faman haɗiyar yawu nake da ƙyar zuciyata na faman kai da kawo a cikin ƙirjina. Umarnin tashi suka bani, bani da ikon yin musu ko dan bindugun dake a hannunsa, ɗaya daga cikinsu ne ya koma ta bayana ya ɗauro ƙyalle a saman idona, zanyi magana ya ce, “Shiii!! Young Lady, inba hakaba harsashi ya rufe miki baki”.      Yawu na sake haɗiyewa mai kauri, daga haka ban sake magana ba har suka bani umarnin tafiya bayan sun saka min wani abu a hannu na riƙe. Tafiya kawai naji munayi batare dana san ina muke nufa ba, amma dai baka jin hayaniyar komai ko'ina tsitt sai kukan tsuntsaye daga ɗan nesa damu kaɗan. Da ace hannuna babu handcuffs wlhy sai na cire abinda aka rufen fuskar komai ma za'ayi ayi. A haka naji mun shigo wani waje mai shegen sanyi da ƙamshi na musamman. Nanma mun ɗan yi tafiya kafin naji mun tsaya cak a inda ƙafata ta taka wani lallausan abu.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒕𝒉𝒊𝒓𝒕𝒚 𝒏𝒊𝒏𝒆_ ......Kamar yanda d.c.o ya nema washe gari an sake kawo masa bayani akan ɗayan daya buƙata. Sai dai abin baƙin ciki shima layin na taƙaitaccen lokaci ne kamar wancan, ba kuma a taɓa kiran wani da shi ba. Nasara ɗaya da suka samu itace na shi wanda yay register ɗin layukan duk mutum ɗaya ne. Kuma a lokaci ɗaya yayisa. Sun saka a nemo musu shi a duk inda yake. Hakama abokin masu napep an samu nasarar cafkosa a safiyar yau. Bayan kamar awa biyu da kawosa police station ɗin aka kaisa office ɗin d.c.o kamar yanda ya buƙata. Sai da ya gama masa kallon tsaf daga sama har ƙasa kafin ya tura masa hoton Samraah dake gabansa.       “Kasan wannan?”.    Ya faɗa kansa tsaye idanunsa ƙyam akan saurayin. Hoton saurayin ya ɗauka ya kalla na kusan sakan talatin, ɗagowa yay ya kalla d.c.o sai kuma ya rissinar da kansa yana ɗan jinjina kai. “Nasanta ranka ya daɗe. Sam-G ake kiranta, tana gabatar da shirin matasa kuma ina ɗaya daga cikin fans nata da shirin baya wuceni ta redio ko shafukanta na sada zumunta  musamman YouTube da ake ɗora shirin, nakan je na kalla videos ɗinta”.         Kai d.c.o ya jinjina masa da faɗin, “Masha ALLAH. Minene sana'ar ka?”.      “Direban napep ne yallaɓai”.   “Kozan iya sanin ranar goma ga watan nan kana ina? Da ga shida na safe har zuwa ƙarfe takwas?”.     Jimm yay irin na mai son tunano abu. Har kusan minti ɗaya sai kuma ya ɗago yana girgiza kansa. “Na manta yallaɓai. Saboda kwanakin sun ja da yawa”.       “Uhhm yayi ƙyau” d.c.o ya faɗa yana kallon yaronsa. “Azo da yaran nan su duka”.    Kai yaron nasa ya jinjina cikin girmamawa. Fita yay babu jimawa sai gashi ya dawo tare da samarin farko da aka fara kamawa. Yanda suke kallon saurayin haka yake kallonsu. Duk da babu duka ko zagi da akai musu zaman waje ɗaya da ɗan karan Dauda yasa duk sunyi wujiga-wujiga dasu....      “Kasan waɗan nan?”.    “Eh yallaɓai na sansu, su duka abokaina ne. Tare ma muke harkar napep ɗin ma.”     “Kace ka manta mi kayi ranar goma ga watan nan da safe ko?”.    “Eh yallaɓai a gafarceni”. D.c.o baice dashi komai ba. Sai abokinsa ya kalla ya ce, “Kai tuna masa”.      Kai tsaye abokin nasa ya ce, “Kazo ɗakinmu ni da ƙanina bayan sallar asuba dan gari ma bai gama haske ba. Kace na baka makulin mashin ɗin Imran zakaje amso saƙo tasha kai taka tayar na gareji dan naka babur ɗin ya samu matsala tun jiya sai barinsa ma kayi ya kwana a gareji kan yau zaka kai musu tayoyi da zasu canja maka. A gaban ƙanina Isa akai komai kuma”.       Da sauri ya dafe kansa ya ce, “Tabbas anyi haka Salisu. Tabbas abinda ya faɗa gaskiyane yallaɓai, amma a gafarceni inada yawan mantuwa ne wlhy. Na amshi mashin ɗin, abinda nace kuma zanyi naje nayi da shi”.       “Masha ALLAH haka muke son ji ai dama. Ina ka kai yarinya to? Sannan waye ya sakaka kidnapping ɗinta? Ko raɗin kanka ne kawai?”.      “Ya salam kidnapping kuma? Ni banyi kidnapping kowaba ranka ya daɗe. Duk wanda ke tare dani kuma yasan wannan ba aikina bane ba inada sana'a. Taya ma kuma na rasa wanda zan ɗauka sai Sam-G”.       “Ƙarya kake yi, a waccan ranar ba gareji kaje da napep ɗin abokinka ba Yakasai kaje layin gidan su Samraah. Kai zaman jiranta na kusan mintuna talatin da huɗu. Zata iya yiwuwa kasan dama zata fito a lokacin ne. Dan haka tana fitowa da shirin tsaida abin hawa kazo ka ɗauketa. Ka tsaya a dai-dai fita anguwar ta titin bayansu gaba ɗaya. Ka cire wayarta da facemask da eyeglasses ɗinta ka ajiye saboda maybe kana tunanin za'a iya ganeka ko kuma wanda ya saka ka aikinne ya baka umarnin yin hakan. Ɗan saurayi ban kawoka nan dan ka raina min hankalina ba. Amma kana da zaɓi guda biyu. Fitomin da komai a yanda yake dan ka samu sassauci ko cigaba da raina min hankali na saka ka faɗa ta dole wanne ka zaɓa?”. Ɗan jimm yay na wasu sakanni, sai kuma ya sauke numfashi da faɗin, “Zan faɗa maka gaskiya yallaɓai.......    🌟(✧✧)🌟(✧✧)🌟(✧✧)🌟       Cikin fisgar zaren da suka ɗaure min ido naji sun warwaresa. Har sai da na ɗan ciza lips saboda yanda naji zafi, amma dai na dake ina mai buɗe idanun nawa a hankali, dan zan gama da ogansu ne sannan na dawo kansu shegu masu suffar bakaken aljanun kan kuka. Sosai gabana yay masifar faɗuwa dan kai tsaye idanuna akan mutumin dake zaune cikin kujera yay crossing ƙafafunsa idanunsa a tab.. dake a hannunsa suka sauka. Ga wani daddaɗan ƙamshinsa da ya cika min hanci da gauraye falon gaba ɗaya. Fuskarsa ciɗin-ciɗin kamar bai taɓa sanin abinda ake kira dariya ba ko saƙon wani bala'i ya riskesa a yanzu. yauma akwai kitso a kansa guda biyu rak da suka zanu tamkar an zana a takarda dan zaka rantse ba hannu ya kitsasu ba, sai farin sirrin gilashi da ya zauna masa ɗaram a fuska tamkar an haliccesa da shi ne. Yatsunsa biyu ya ɗan juya, da sauri sangama-sangaman samarin nan da suka rakoni da bindiga duk suka fice aka bar abokin cin mushen nasa kawai. Sai lokacin ya ɗago ya zuba min cat eyes ɗinsa. Kallon ido cikin ido mukaima juna. A take naji ciwon marata na neman dawowa sabo fil, ba shiri nai saurin duƙar da kaina ƙasa zuciyata na wani kalar masifaffen bugu kamar zata faso ƙirjina ta fita. Amma cikin ƙarfin hali na murguɗa masa baki bayan na saukar da idanun.      Shima janye nasa yay cikin yanayin isa da ƙasaita. “Sit!” ya faɗa a daƙile yana maida kansa ga tab ɗin tasa. Duk da na gane dani yake banyi abinda yace ɗin ba har sai da yaronsa ya sake maimaita min a ɗan tsawace. Ta ƙasan ido na hararesu su duka, kafin na kai zaune saman lallausar kujerar falon, amma sai yaron nasa ya daka min tsawa da mun nuni da wai na zauna ƙasa. (Munafuki ɗan baƙin ciki) na faɗa a raina, a zahiri kam hararsa na sake yi sannan nayi yanda yace na zauna ƙasan carpet ɗin da ko makaho ya laluba yasan ya haɗu. Jikina na ɗan takure a waje ɗaya, na tallafo ƙafafuna duka da hannayena biyu idanuna na kallon carpet ɗin. Sai da kusan mintuna uku suka sake shuɗewa babu alamar zai sake magana, sai kuma a cikin daƙilalliyar muryar nan tasa ya ce, “Wa kike ma aiki a kaina?”.         Sosai tambayar tai matuƙar bani mamaki, har takai na ɗago na ɗan kallesa. Amma a mamakina bama ni yake kalloba, wasu files ne a hannunsa yan rubutu a ciki ya ajiye tab ɗin yanzu. A hankali na maida kaina na duƙar, nima sai da na kwashe wasu sakanni kafin cikin siririyar muryata da yanayin gafara na bashi amsa, “Ni nafi ƙarfin yima kowa aiki ai, dan ni ma ɗin gayyace”. Shiru baice komai ba, dan haka na cigaba da ƙunƙuni ƙasa-ƙasa batare da tunanin zasu ji ni ba. (Ni ai nafi ƙarfin aiken wani, sai dai zuwan kai da kai. Dan TSUTSAR NAMA ITAMA NAMA CE ai. Idan kuma baka san haka ba kaje kayi bincike. Ashe ma matsoraci ne, tunda har baka iya fito na fito sai ta YAƘIN SUNƘURU...)        Harara yaron nasa ya zuba min. Kafin cikin kakkausar murya ya furta, “Hattara dai ƴammata. Dan ba'a ado da furuci wani lokacin takobin yanka wuyan mai shi yake zama. Nan ba gidan jarida bane, fadar SARKI ce mai cikakken iko kike.”       Murtanin harar nima na maida masa ƙasa-ƙasa. Sai dai na gagara iya cewa komai saboda yanda ogan nasa ya tsareni da shegun kaifafan idanunsa na maguna. Tsahon lokaci falon shiru, yayinda tuni ya janye idanun ya maida ga abinda yake yi. Sai zuwa can a wani irin daƙile ya furta, “A duk sanda wani ya nema shiga min hanci nakan ji farin ciki da mazantakar fyatosa. Shiyyasa abinda yafi birgeni a duniya sune mutane irinki masu taya business ɗin da bai shafesu ba. Well ba tabbatar miki da ni waye yasa nasa a kawoki nan ba, dan inada tarin ayyuka na kai da kai matuƙa. WAYE YA AIKO KI WAJENA?”.        Takaicin maganganunsa yasa bamma san sanda na furta, “Umarnin kaina nake bi ni, na kuma faɗa ai”.      A harzuƙe yaronsa ya katseni da faɗin, “Be careful ƴammata. Walƙiya ba tana nufin ado ne kawai ga sararin samaniya ba. Takan zama gargaɗi ga ma'abota shagala ne. Jirgin ƙasa duk ƙawatuwarsa a hanyarsa kawai yake iya tafiya, saɓanin hakan faɗuwar baƙar tasa zaiyi ta yanda ko kufansa bazai moru ba balle ma'abota shiga cikinsa. Ki dinga bambance tsakanin sama da ƙasa a duk lokacin da kikai tunanin hawa tsani da tunanin taɓa rana ko farin wata. Dan batun wanda zashi sama ya taka leda zance ne kawai irin na masu iya magana.”        Baki na laɓe tare da watsa masa harara ta ƙasan ido. Cigaba yay da faɗin, “Kina da zaɓi biyu, bada abinda ke hannunki ki koma ki cigaba da rayuwarki cikin salama, ki kuma sakama ranki baki taɓa ganin komai ba a wacan ranar, ko nuna taurin kai ki dawwama anan har ƙarshen numfashinki, kin buƙaci 500m an baki rabinsu, amma ke kin kasa cika naki alƙawarin duk da an tabbatar miki idan kin bada za'a baki sauran 250m ɗin. Ke kin san kuwa dawa kike tare ana?”.      Yanzu kam sosai na ɗago a razane matuƙa, tare da wurga masa hararesa dan naga yama fi ogan nasa zaƙewa. A kausashe nima na ce, “Lallai baka da hankali. Ni nace ku bani 500m?........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚_ .......A kausashe nima na ce, “Lallai baka da hankali. Ni nace ku bani 500m?. Aikin naku ya wuce kisan kai da kidnapping harda sharri kuma. Lallai tatsuniyar gizo da ƙoƙi kenan young man, kasan kuwa gaibu ce dan hikimace kawai irin ta masu iya zance da rubuta hikayoyi. Idan har ka yarda ba'a mutuwa a dawo, to ka ɗauka abinda duk yake a hannun Samraah Gwarzo mallakinta ne ita kaɗai, ko a mafarki bazan taɓa cinikayyarsa da wani ba. An gaya maka nima faƙiriyace bana neman na kaina ne da zan zauna neman a bani fansar kuɗin jinin mutane akan video?. ALLAH ya sawwaƙe, Banyi lalacewar baƙar tasa ba ai, banga kuma wata dukiya da wani zai tara taja hankalina ba dan nima dai kasuwancin nan inayinsa. Ɗan jarin nan na dubu ashirin da ake rainawa na tara wataran sune zasu koma miliyan dubu ashirin ɗin. Dan haka kuma nema wanda ya amsa kuɗinku tun wuri amma ba ɗiyar Abdul-wahab ba. Idan kuma kaine ke yawo da hankalinsa ka faɗa masa gaskiya inma dan kaga baya jin Hausa ne, oho can dai muku matsalarku ce ma wannan dai. Dannni idan har Yaya Musaddiq da Mansoor na numfashi a duniya na maka alwashin nan da kwana takwas iyanzu ina can a tsakkiyar dangina suna shagalin taron bikin aurena tare da ni, yayinda ku kuma zaku kasance a police station kuna amsa tambayoyi”.        “Yaro bai san wuta ba sai ga taka”. Yaron nasa ya faɗa    “Babba bai san yaro ba sai ya latsa”. Na bashi amsa nima a kausashe ina sake balla masa harara kamar manyan idanuna da ke nuna yanayin bana jin daɗi zasu zubo ƙasa. Juyawa nai shima ogan nasa zan hararesa sai naga ya zuba min ido kamar wanda yay zurfi a tunani. Ban fasa hararar tasa ba, dan haka na maka masa kawai na ɗauke kai ina ƙunƙuni ƙasa-ƙasa (Garama ku sakan tunkan kuja a saka sunanku cikin jerin manyan ƴan ta'addan duniya dan wlhy tona muku asiri zanyi ni babu ruwana).       Tsawa yaron nasa ya daka min alamar ya jini, duk da na tsorata amma mai kicin-kicin da fuska naƙi nunawa. Kuma bakina bai bar motsin ƙunƙuni ba. Wani shegen murmushi ogan nasa da tun maganar farko da yayi bai sake nuna yama san da zaman mu a falon ba ya saki. Tare da lumshe idanunsa cike da salo luuuu ya kuma buɗesu a slowly warrr. Batare da ya sake furta komai ba ya miƙe abinsa ya nufi wata hanyar gilashi data mamaye kusan bango guda na falon har kana iya hango ƙyawawan korayen ciyayin dake ta waje da ga nan, fita yay abinsa cikin wani irin takun mazantaka da nuna ƙarfin iko.....         Wata ƴar siririyar dariyar da yaronsa ya saki ta sakani kallonsa. Ya rumtse hannunsa tare da nuna babban yatsar hannunsa kasa👎 yana wani ɗaure fuska ya furta, “Lallai na tayaki jaje ƴammata. Dan kin taro babban match da baki da defenders balle ƴan kallo. Tunda har kika bari boss ɗina ya taya wannan wasan sai kinyi dana sanin da sai tafi biliyan a cikin koguna biliyoyi. Dan shi giwa ne baya WAIWAYE. Sannan zaki ne ba'a gaba da gaba da shi. Ki jira TAKUN FARKO na wasan kawai, tun anan zaki raina kanki.”        Baki na laɓe nima, tare da watsa masa harara. Cike da tsiwar ƙarfin hali na ce, “Shi kaɗai ka sani da dukkan salonsa. Abinda kuma ni zan iya sirrina ne, kaga kenan tsakanin ni da shi ba'asan maci tuwo ba sai miya ta ƙare a wasan. Dan haka ina baka shawara tunda kaine abokin sharrin nasa. Ka gaya masa da gaggawa ya maidani inda kuka saka aka ɗakkoni, idan ba haka ba, wlhy sai kunyi dana sanin shiga sabgata. Dan zan ajiye muku tarihin da bazaku sake gwada cutar da wani ba bayan ni. Koda kuwa kasheni kukayi fatalwata bazata barku ku zauna lafiya ba. Dan nasan abinda kuka iya kenan kashe mutane kuyi tsafi da jininsu ko”.         Dariyar kularwa ya saki da faɗin, “Irinku dama boss yafi buƙata a wasa. Kema shaida ce tunda a gabanki ga faɗa da bakinsa. Tunda kin shirya game ɗin ga fili ga mai doki, ni dama nawa shawara ce. Kuzo ku maidata inda kuka ɗakkota”. Ya ƙare maganar ƙarshe cikin ɗaga murya. Baima gama rufe baki ba sai ga garadan ɗazun sun shigo kuwa..      (Tofa, Samraah miya faru kuma bayan hakan?).   Humm Bily komai ma ya faru, dan zan iya ce miki a wannan gaɓar ma ne labarin ya ɗauki dai-dai saitin inda kowa ya kamata ya fahimci raunin daya taɓani da kuma nasarorin dana samu. Dan komai da kika ji a baya dai-dai yake da sharar fage. Konace shimfiɗar labarin. Amma kundinsa wannan gaɓar itace SHAFIN FARKO. An maidani ɗakin da aka fiddoni kamar yanda yaronsa ya bada umarni. Da ga haka ban sake ganin kowannensu ba. Sai dai ana kawo min abinci sau uku a kowanne rana. Kamar yanda na kasance a kulle a wancan gidan nan ɗin ma hakanne. Sai dai akwai masu tsarona anan, kuma na nan sun ma fi nacan firgitarwa. A ƙuntace nake matuƙar ƙunci, ga ciwon jiki dana zuciya. Ga kewar ahalina data masoyi. A kowane cikar minti ɗaya na agogo sai na lissafa sauran daƙiƙun da suka rage na cikar ranar aurena. Hakan yasa a duk sanda tunani ya nema fasan zuciya zaki sameni ina karatun Alkur'ani ne. Ina jin sauƙi sosai a raina, bayan na koma yin salla ma Alhamdullah na sake rungumar ibada ta. Dan akoda yaushe cikin kaima UBANGIJINA kukana nake. Ina kuma jin yaƙinin zai karɓa min.. Zakisha mamaki idan nace dake maganar da yaronsa yay na cewar na buƙaci su bani 500m kuma sun bada 250 a cewarsu ban wani sakata a raina ba. Danni a nawa wautar kawai sun faɗane bisa raɗin kansu da son min barazana ne dan na basu abinda suke son, dan haka na cigaba da harkar gabana kawai na manta da duk wani gargaɗinsu balle zuciyata ta fara min wani hasashe mai muhimmanci daya kamata ace nayi, ban san rashin yin shine zai zame min babban kuskure ba kuwa. Dan da'ace nayin maybe da abubuwa basu kasance a wani matsayi daban taɓa tsarama kaina ba bisa ƙaddarar rayuwa. Karna cikaki da zance muje zuwa dai.....        💞☞💞☞💞☞💞         “Ranka ya daɗe zan faɗi gaskiyar abinda ma sani. Sai dai yanda ka fahimci al'amarin sam ba haka yake ba. Wlhy wlhy duk abinda zan faɗa maka shine gaskiyar abinda ya faru. Tsoro ya hanani faɗar gaskiya tun ma a farkon fara case ɗin. Amma na gwada yin hakan tun sanda naji zancen ɓatar Sam-G da kuma kama Salis da akai. Ni bani na saceta ba, hasalima ban san ita za'a ɗauka ba. Wanda kuma ya ɗauketan wlhy ban san kidnapping ɗinta zaiyi ba. Kamar yanda na sanar ma abokina Isa da gaske na amashi mashin ɗin Salis ne a hannunsa domin zanje amsar sako tasha da aka turoma Mamana daga Maiduguri, da kuma tayoyi da za'a sakamin a nawa daya samu matsala. Na fito titin anguwarmu kaɗan wani bawan ALLAH ya tsaidani, banyi niyyar tsayawarba, saboda ina da uziri, ban fitoba kuma domin yin aiki ba. Gashi kuma safiya ce sosai dan ko haske gari bai gama yi ba. Sai dai ganin dattijo ne mutumin yasa naji tausayinsa. Dan harma na gotashi na dai dawo, tambayarsa nai inda zaije, dan naji ko yayi dai-dai da inda na nufa. Amma sai da ya shigo ya zauna yake gaya min. Ga abinda yace min da yasa na ɗaukesa tilas badan naso ba. (Yaro dan ALLAH ka taimaka min, Yakasai zanje, yarinyatace take da lalurar aljanu, jiya da dare muka nemeta muka rasa, sai ɗazun nan da asuba ƙanina yay kirana tana gidansa ta kwana acan Yakasai ɗin. To munsan zata iya barin nan ɗin akoda yaushe, kuma idan suka kaɗata bamu san ina zataje ba. Yanzu ma ko gidan bazamu ƙarasa ba zamu ɗan tsaya ne a kan layi data fito mu mata wayo, zan kira ɗan uwanta da zarar mun ɗauketa sai yazo ya ɗaukemu dan in kai tsaye ne bazata yarda ta shiga motarsa ba, amma idan na shaƙa mata maganinta zamu samu nasarar yin hakan). Yanda dattijon ke magana yasa na amince da shi, dan sam baiyi kama da wanda zai yi ƙarya ba, gashi kuma a cikin kamala. Lalura kawai daya kira yasa nai tunanin taimaka masa, dan nima ƙanwata nada irin makamancin lalurar, na kuma san irin tashin hankalin da muke shiga. Cikin nuna damuwa nai mata addu'ar samun lafiya, sannan na sanar masa gaskiyar ba aiki na fito ba, amma idan bazamu jimaba zan taimakesa, sai dai idan ta jima bata fito ba zan sakashi a wata napep ɗin ni na tafi uzirina dan abokina na jiran napep ɗin sa. Babu musu ya yarda da hakan har yana jeramin addu'oi ga hawaye yana faman yi. Ni dai na bashi haƙuri muka ɗauki hanya. Mun isa Yakasai, shine kuma ya nuna min inda zan tsaya, shi kuma ya fita ya maƙale a ɗan nesa dani. Nayi zaman kusan mintuna ashirin duk naji na ƙosa dan babu abinda nake sai faman tsaki, ina ma niyyar barin wajen ne sai gashi da saurinsa yake sanar min gatanan zuwa, dan ALLAH na taimaka kada na bari ta shiga ko wane mashin sai nawa. Yanda naga yana rawar jiki ga hawaye yana sharewa da gefen rigarsa yasa naji tausayinsa, duk kuma yanda ya tsara haka nayi. Mun fito a wajen mai saida lemo da aka tsinta wayarta daka faɗa yace na tsaya ga ƴaƴanta a mota.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒐𝒏𝒆_ .....Hakan kuwa akai na tsaya dai-dai motar dake a fake, wanda akace Yayanta ya fito cikin nuna alhini yana min godiya, su biyu suka kamata suka saka a motar, ni sai lokacin ma na lura sun shaƙa mata maganin da yace, amma sai ban kawo komai a raina ba tunda dai dama yace zai saka mata magani. Yayan nata ne ya bani kuɗi masu yawa, nace masa bazan amsa ba ni dan ALLAH nayi, kuma ma ai kuɗin daya bani sun wuce na hakkin aikina. Murmushi kawai yamun ya ajiye kuɗin ya faɗa mota. Daga haka suka wuce suka barni ina kallon kuɗin, wlhy ban san sun yadda wayarta da facemask harda eyeglasses ba. Kuma suma ina ƙyautata zaton basu san sun faɗi ba kuskure kawai aka samu maybe. Suna wucewa nima na wuce, ban kuma san mike faruwa ba sai da yamma nake jin labari, abinda ya tada min hankali shine yanda ake misalta al'amarin yayi dai-dai da abinda ya faru da safe ni da dattijo, washe gari kuma sai naji batun kama Salis dangane da napep ɗinsa. Wlhy iya abinda nasani kenan, amma banda alaƙa da ɗaukar tata nima sai da naji daga baya hankalina ya tashi wlhy. Dan da nasan abinda zasuyi kenan babu yanda zan taimakesu, idan ma naga sunfi ƙarfina zan kira ƴan sanda. Dan ka tambaya kaji munsha irin wannan taimakon, adalilin haka har karyani an taɓayi abokaina gasu nan shaida ne”.          Shiru d.c.o yay na wasu mintuna kamar mai nazari, sai kuma ya sake kallonsa ya ce, “Zaka iya gane mutumin da saurayi yanzu idan ka gansu?”. “Tabbas zan iya ganesu musamman ma dattijon duk da ya saka hirami a kansa ranka ya daɗe”. Kai kawai d.c.o ya jinjina batare da ya sake cewa komai ba ya bama yaransa umarnin a maidasu cell. Hakan kayi, bayan an maidasu ya zauna da yaronsa dake kan case ɗin.     “Ɗan Bakori mika fahimta a zancen yaron nan?”.    “Ranka ya daɗe al'amarin ne akwai wuyar sha'ani, amma dai kamar akwai ƙamshin gaskiya a zancen nasa. Wani abu dana fahimta shine amfani kawai akai da shi, kuma tabbas in har da gaske bashi da hannu duk waɗanda sukai abun to sun sanshi dan dole sunada kusanci koda ta zaman anguwa ne. Shiyyasa sukai masa wayo da batun iska tunda sun san ƙanwarsa na fuskantar irin matsalar zai fi saurin afkawa. Zancen daya faɗa ya taɓa samun karaya akan taimakon wata yarinya kuwa gaskiya ne. Dan na samu wannan labarin a binciken da nayi tun a farko. Mutanen na shegune suna da wayo, kuma sun shirya komai yanda suke so kafin su tunkaresa. Abu na ƙarshe bana raba ɗayan biyu duk wanda yay aikin nan na jikinta ne, ta sanshi ya santa sosai, dan inba haka ba tayaya suka san zata fito a lokacin tunda ba ranar aiki bace ba?”.          “Tabbas zancenka na akan hanya ɗan Bakori. A wannan gaɓar dole aikinmu ya ɗan sake komawa baya kaɗan. Wayarta da aka tsinta daga biyar na yammacin ana gobe abin zai faru har washe gari a duba dawa tai waya? Waye yay kiranta? Koya turama saƙo koya turo mata.”      “Okay Sir, amma naji kamar Yayanta yace da waya biyu take amfani, kuma sun wuce da ɗayar”.     “Wannan ba damuwa bane, duk da dai ta wani fanin kasancewar wayoyin duka biyu zai fi mana. Amma ɗayar ma zata taimaka mana. Dan kamar yanda yaron nan ta faɗa sam basu san sanda ita wannan wayar ta faɗi ba kuskure aka samu. Itama in sha ALLAHU zamu samu abinda zai taimaka mana ku bincika”.     Cike da gamsuwa ɗan Bakori ya miƙe tare da yin salute ɗin sa sannan ya fita da sauri....         💥💫💥💫💥💫💥 Ɗan taku yake cikin kai-kawo babu alamar rikicewa ko shiga wani yanayi a tare da fuskarsa a bayyane. Sai dai a can ƙasan zuciyarsa auna komai daya fita daga bakin Samraah yake kalma bayan kalma. Tare da ajiye kowanne word a mizanin hankali. A wannan yanayin Hayatu ya samesa. Ganin a yanayin da ogan nasa yake sai ransa ya ƙara ɓaci shima, dan haka a harzuƙe ya ce, “Sir yarinyar nan fa nada ɗan banzan wayo, ga bakinta kamar reza baya mutuwa. Ƙarya take tasan komai tana pretending ne kawai. Ba gashi yaron nan da aka amsheta a wajensa yace itace ta sakashi yay kidnapping ɗinta Dan ta bada ƙafa......” Wani irin murmushi Maash daya kafa masa ido ya saki a karo na farko, sai kuma ya girgiza kansa kawai tare da janye idanun ya maida kan ƙyawawan firannin fulawoyi da aka ƙawata wajen da su, baka jin komai sai daddaɗar iskar da suke badawa da ƙamshinsu a wajen. Shiru bashi da niyyar cema Hayatun komai har shi Hayatun ya ƙosa da shirun nasa duk da ba sabon abu bane a wajensa. Dan inma bai gadama ba zai iya sharesa yaƙi cewa komai kuma shikenan amsar tabi ruwa. Sun kai tsahon mintuna uku a haka kafin cikin silent voice ɗinsa a can ƙasan maƙoshi a daƙile ya furta, “Hayat be a man mana. Kullum ina sanar maka ka dinga lissafi akan abubuwa. Amma na fahimci brain naka harkar business kawai take iya ganewa. Mizai hana a duk sanda baka fahimci miya dace akan abu ba ka dinga bashi lokacinsa dan ka fahimta. Ina matuƙar tsoron kada maƙiyan dake bayana suyi amfani da wannan ruɗanin naka da rashin hange wataran su ci nasara akan ka. Yarinyar tanada tsiwa da raini. Sannan harshenta nada kaifi. Zan mata hukunci dai-dai da wautarta. Kuɗina kuma nasan inda suke, zakuma su dawo nan bada jimawa ba batare da rasa ko naira ba a cikinsu. Video kuma dake hannunta muna farautarsa ne mu da su a hannunta, sai dai basu san MAASH ba shashasha bane irinsu. Zan tabbatar musu kuma da hakan, dan a matakin wasan farko da su zan fara buga game ɗin kafin na dawo kanta. Ka siyama Sani ticket a yau ɗin nan ya biyo jirgi zuwa Abuja. Hakama Abubakar ina son ganinsa yau da dare”. Daga haka ya juya ciki batare da ko waiwayen Hayatu ba. Da kallo Hayatu ya bisa galala kamar idanunsa zasu zubo. A zuciyarsa ya shiga faɗin, (Idan nace mutumin nan Aljani ne ace ba haka ba. Yanzu dan ALLAH duk wannan zaƙewar da nake dama ni yakema kallon wawa? To wai tsaya ma. Shi abinda ban gane ba anan. Kuɗi dai ni aka saka na turasu a account no.. da mutumin ya turo. Kuma ni da shi mun tabbatar da sabon account ne aka buɗe muna saka kuɗin kuma aka ciresu tare da blocking account ɗin ma gaba ɗaya. To shi tayaya ya bibiya ya gano komai? Mutumin da kullum damuwarsa maida naira ta zama dala. Kai nikam fa na fara tsoron boss ɗina. Ko yanzu ma ji nake zazzaɓi na nemam rufeni, dole ne sai naje asibiti naga likita). Ya ƙare zancen zucin nasa da kai hannu ya taɓa goshinsa da wuyansa kamar wani ƙaramin yaro. (HAYATU na buƙatar ganin dacta. Likitocin gidan nan ku fito ku bashi agaji🤣😂🙏) 💞✨💞✨💞✨💞      A lokacin da ƴan sanda keta nasu ƙoƙarin, a ɓangaren Yaya Musaddiq shima yana can tare da su Kawu Musa da sukazo da ga Gwarzo. Ba wannan ne zuwansu na farko ba. Sun dai sake dawowa ne suji yaya ake ciki duk da suna waya da Musaddiq ɗin akai akai game da al'amarin. Da ƙyar Mum ta yarda ta basu abinci, dan saida ma Abba ya nuna mazantaka yau. Bayan sun gama cin abincinne suka zauna tattauna abinda ya kawosu. Kawu Lurwani ne ya fara magana alamar shi suka wakilta yayi. Sai da ya kalla Abba da Musaddiq sannan ya fara faɗin. “Wato Imamu magana ce mai muhimmanci ta kawomu nan tare da sake jajantama juna akan batun yarinyar nan. Al'amarin nata akwai mamaki da ban tsoro ƙwarai matuƙa. Dan zuwa yanzu dai duk mai hankali ya kamata ya fahimci ba waɗan nan mutanen bane masu cewa a basu kuɗi idan sun kama mutum. Dan da ace hakanne da tuni sunyi maganar kuɗin. Amma gashi yau har kwanaki goma sha uku da rasata babu wani bayani. Hakan na nufin aikin magautane tunda yarinya ce mai farin jinin mutane sakamakon aikinta. Yanzu mu kai tsaye bazamu ce ga wanda yay wannan aika-aikar gareta ba damu ma kammu da ke a cikin tashin hankali. Bamu ce kuma ƴan sanda sun gaza ba, dan suna iya ƙoƙarin su suma. Amma magana ta gaskiya bai kamata muma mu rungume hannu muna jiransu ba.....”       “To Lurwanu yaya zamuyi idan ba hakan ba. Aikinsu ne ai, sune kawai suke da dabarun bincike, dan a yanzu haka since wanda ya ɗauke ta a napep yana hannunsu ma, sai dai yaƙi amsa laifinsa”. Abbane yay maganar cikin katse Kawu Lurwanu. Kai Kawu Lurwanu ya girgiza, “To ai ban kai ƙarshe ba nima ka katseni Imamu, abinda nake so nace bafa zama zamuyi mu rungume hannaye muna jiransu su kaɗai ba. Kamata yay muma mu saka roƙon ALLAH tako ina. Sai dai kasan mu ɗin ba masu ƙarfi bane, kuma al'amarin yana buƙatar sadaka. Dan haka muka yanke hukuncin dawo da waɗan nan kuɗi na aurenta da aka karɓa, dan dubu ashirin kawai mukaci a ciki aka ajiye tamanin akan idan lokaci yayi zamu ƙara da wasu a rage maka hidima. Kaga kaima saika kawo wani abu daga cikin wanda ke hannunka a haɗa a sai abinci da wasu abubuwa aita sadaka ana addu'a sai kaga anci nasara ALLAH ya bayyanata cikin sauƙi. Dan yarinyar nan kullum kwanakin bikinta sake matsowa sukeyi, dan ma yaron kirki ta samu, kuma danginsa basu da fitina, amma wlhy da wasu ne da yanzu sun fara zame-zame akan al'amarin nan. Amma kaga yaron nan da shi aketa faman faɗi tashi na son ganin an samota har ma da iyayen nasa. Amma yaya ka gani shawara ce?”.        A ɗan fusace Abba ya ce, “Ni gaskiya babu kuɗin nan yanzu a hannuna. Sai dai idan shi Musaddiq nada su ya aramin idan na samu zan bashi”.      Kaf falon babu wanda bai ƙwalalo idanu waje dan mamaki ba.......✍️       _Ai ni kaina idanun nawa a waje. Abba al'amarin ka ya fara ban tsoro da mamaki. Ya rabbi kasa mu rayu da ƴaƴanmu, maraici da banne wlhy a rayuwa😭_. _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒘𝒐_ ........ Musaddiq ne kawai yay murmushi yana mai girgiza kansa. Ganin Kawu Musa na neman fusata dan dama shi akwai zuciyar tsiya yay saurin faɗin, “Uhm Kawu inaga babu damuwa ai. Kuma na wajenku ku barsu. In sha ALLAHU babu abinda zai gagara na sadakar. Ko daga gobe in ALLAH ya kaimu ake son fara duk abinda ya dace ni a shirye nake.”      Sosai suke kallonsa zukatansu na ƙara rauni. Yaron jarumine na gaske da kowaɗanne irin iyaye zasu yi alfahari da shi. Gaba ɗaya halin Musaddiq irin na mahaifinsa ne. Ga sanyin hali ga haƙuri ga kirki da jarunta. Sun nuna masa zadai su bashi kuɗin amma ya dage kan bazai amsa ko sisi ba. Dole suka haƙura suka barsa. Ƙyawawan halayen yaron na sake saka musu jin kunyar wofamtar dasu da sukayi a lokacin da suke matuƙar buƙatar tallafinsu, amma kuma bakin alƙalami ya riga ya bushe yanzu kam sai dai haƙuri, dan ta wani ɓangaren suma ba laifinsu bane. Ƙanin mahaifiyarsu ne ya nuna musu shi ɗan boko ne kawai sjiyyasa sukai zuciya suka bar masa su.         Kaf abinda ya faru a zaman sai da Mum ta tsare Abba ya sanar mata. Aiko ta sake zugesa akan babu wata addu'a sun zo ne kawai su yaudaresa su amshi kuɗin. In ba hakaba wace addu'a ce za'a wani ce sai da kuɗi. Daga ƙarshe ta sake ingizashi kan ya binciki Musaddiq duk yanda akai yaron kuɗine da shi, in ba hakaba taya komai ya taso sai yace zai yi. Daram kuwa ya hau ya zauna ko kunyar ALLAH babu washe gari yay kiran Musaddiq yay masa tujara. Ya kuma ce yana buƙatar 1mil a wajensa da za'aima Samraah kayan ɗaki, sannan ya bada kuɗin kayan kitchen suma Mum zatayi masa list ɗin komai. Sai da ya gama sauraren Abba kaf sannan yay murmushin sa mai sanyi. Cikin nuna rashin wata damuwa a fuska ya ce, “Ba damuwa Abba ka saurareni zan samo in sha ALLAHU”.       Sallamarsa Abba yay yana ƙara jaddada masa. Yana fita Mum tai wuff ta fito alamar dama laɓe tai musu. Zama tai kusa da Abba tana faɗin, “Bana gaya maka ba Abban Abbas. Yanzu ka yarda ko? To ALLAH kaɗai yasan mi yaron nan ya tara yake raina mana wayo ya barmu da nauyin hidimar rawuwarsu. Ana gama hidimar bikin nan ya kamata ka sashi ya bama Abbas jari yabar wannan gantalin rashin aikin, sannan itama Baby ta fito da miji dan nagaji da yawon nan nata haka nan”.          Babu wani dogon nazari ko tunani a wannan magana Abba ya amsa Mum tare da bata goyon baya ɗari bisa ɗari. Daga haka suka cigaba da hirarsu cike da soyayya.    A ɓangaren Musaddiq kam shi al'amarin su Abba kam ya fara bashi tsoro. Dan ya wuce abin mamaki ko al'ajabi. Amma dai a wannan karon zai ari halin Samraah ko kaɗanne ya gani ko zasu fahimci shi ɗin bawai sakarai bane. Yana binsu ne kawai da halayensu saboda wasu dalilai. Yanzu banda rashin adalci bama damuwarsu ɓatar ƴar uwarsa ba kusan sati biyu kenan, shi dama gani yake Mum da Baby kamar farin ciki suke da rashin Samraah a gidan. Ko mi tai musu haka da zafi oho ya kasa fahimta. Yasan Samraah fitinanniya ce, to amma duk abinta saika shiga sabgarta ne, kuma mafi yawan lokaci sune ke fara takalarta ita kuma ta maida murtani.       Washe gari kamar yanda suka tsara aka fara gudanar da addu'oi. A masallatai da islamiyoyi, aka kuma dafa abinci aka dinga rabawa mutane musamman ƙananun yara da almajirai. Dan har tsangayoyi aka kai abincin ma. Acan gwarzo ma su Kawu Musa abinda sukai ƙoƙarin yi kenan da kuɗin da Musaddiq ya basu. Dan Mansoor ya taimaka musu sosai da yaji shirin nasu. Dan ko abincin nan ma da aka dafa anan shine ya bada aka dafosa da taimakon Mamynsa.        Kwana uku anata addu'oi da raba dafaffen abinci. Ga kwanakin biki nata sake matsowa daf. Gefe Musaddiq nata wasan ɓuya tsakaninsa da Abba da Mum. Yayinda su kuma suke zaman jiran a kawo musu kuɗi.....         ✨★✨★✨★✨ Tabbas duk wanda ya miƙa al'amarinsa ga UBANGIJI babu shi babu taɓewa Bily, naga fa'idar hakan ƙwarai da gaske a wannan gaɓar. Domin kuwa duƙufar da nai wajen gayama UBANGIJI damuwata ya saka min ƙwarin zuciya da jin sabon ƙarfi na dawo Samraah ta tada. A daren da nake lissafin kwanakin aurena da Mansoor saura biyar kacal a bazata naji ana ƙoƙarin buɗe ɗakin da nake. Hakan ya bani matuƙar mamaki dan ba lokaci bane da ake kawo min abinci, kusan ƙarfe goma da wasu mintuna ake yanzu na dare. Hijjabina daya kasance ɗaya jal da nake salla da shi na ɗauka da sauri na saka. Bamma kai ga ƙarasa sakawarba har an riga an shigo. Baki na buɗe cikin ɓacin rai zanyi magana kawai ya jefamin wata muguwar harara. Ba kowa bane face yaronsa ɗin nan mai dogayen kunnuwa uwa na zomaye. Nima hararsa nai da mare baki, a fili na furta, “Daka daina burga dan baka da banbanci da damisar takarda. Kullum kana bayan wani kamar mai gadi”. A take fuskarsa ta rine zuwa ɓacin rai, ya ɗaga hannu kamar zai ƙwaɗan mari sai kuma miya tuna oho masa ya fasa. Ya dunƙule hannun yana ɗan kaima iska naushi a cikin takaici. Ni dariya ma ya bani, amma sai na dake banyi ba. A cikin zafin rai ya furta “Shigo ki mata”. Ban gama hahimtar mi yake nufi ba likitar ranar data dubani akan matsalar ciwon mara ta shigo. Matar ƴar gayuce sosai. Da gani kuma kasan itama ƴar masu kuɗice. Murmushi tai min cikin tsokana tace ashe dai patient ɗina ta miƙe?”. Watsar da ita nai kamar banji mita faɗa ba, dan haka kawai bata mun ba, nama ɗauke kaina gaba ɗaya. Magana tai yunƙurin sake yi mai kunnen zomaye ya dakatar da ita cikin magana zafi-zafi ya ce, “Doctor kimata kawai”. Itama amsa masa tai da to tana zaro syringe. Kambu idona idon allura na zabura zan miƙe, sai dai mi jinai kawai an damƙomin hannu an riƙe, kafin na farga ta saka min handcuffs. Ido rufe na buɗe baki zan balbaleta da masifa ta shamaceni kawai sai shigar allura naji a hannuna. Kafin wani dogon motsi ta zareta tana sauke ajiyar zuciya kamar daga jikinta take cirowar. Kaina ne ya fara juyawa na koma ganin ɗakin da su kansu bibbiyu, da ƙyar na iya ɗaga hannu ina nunasu amma na kasa magana. Dan idanuna lumshewa suke kaina na ƙara nauyi, a cikin abinda bai wuce minti ɗaya da wasu sakanni ba komai ya koma min ɗiff. Sai buɗe idanuna nai na ganni a inda banyi zato ko tsammani ba....       💫💥💫💥💫💥💫     Duk da tasowar hadari mai ƙarfi na farkon damuna bai hana Musaddiq tashi ba jin an ƙwalla kiran sallar asubahi. Ya fara alwala aka fara yaf-yaf na yayyafi. A gagauce ya ƙarasa ya wuce massalaci. Kamar jira ruwan nan yake a idar da salla ya fara sauka da ƙarfinsa. Kusan duk wanda ke a massalacin da gudu-gudu ya fita domin shiga gida. Hakance ta kasance tsakanin Yaya Musaddiq da Abba. Kusan a tare suka ja wani bahagon birki a ƙofar gidan sakamakon cin karo da abinda basuyi tunani ba ko zaton gani haka. (Tabbas Samraah ce ba gizo bane, ba kuma mafarkin daya sabayi bane ba). Musaddiq ya ayyana a zuciyarsa dake faman gudu da uban sauri a cikin ƙirjinsa. Da sassarfa ya ƙarasa inda take. Dai-dai nan ta fara motsa jikinta sakamakon ruwan sama dake sauka da ƙarfi. Kuka Musaddiq ya saki tare da durƙushewa a gabanta. Gaba ɗayanta ya wawuso ya rungume a jikinsa. Hakkane ya saka Abba dawowa hayyacinsa shima ya nufesu. Cikin rawar murya data jiki ya furta, “Musaddiq da gaske Samraah ɗin ce?”. Bai jira amsarsa ba shima ya kai durƙushe gabansu. Duk wanda yazo gittawa ya gansu sai ya tsaya. Kafin kace mi maƙwaftansu sun ɗan taru a wajen. Duk mazane da aka dawo daga massalaci. Maƙwafcinsu da suke katanga ɗaya ne ya bada shawarar a shiga da ita cikin gida. Wannan shawara tasa ta saka Musaddiq miƙewa ɗauke da Samraah. Ta farfaɗo amma bata iya banbance komai kamar wadda ke a buge cikin maye. Wannan yanayi nata yasa da yawan wanda suka taru a wajen ransu ya ɗarsu da abinda bashine ba.      Abba ne ya shiga kwala kiran sunan Mum. Sai gata a firgice. Da alama ma ita sai yanzu take tashi sallar. Su Baby ma ihun Abban ne ya tashesu a nasu barcin suma duk suka fito. Kowa yaci karo da Samraah sai yay wani irin ja da baya yana zaro idanu. Musaddiq ne kawai keta ƙoƙarin ganin ta buɗe idanunta da take lumshewa da buɗewa da ƙyar tamkar me maye. Kusan mintuna biyar kafin ta buɗe idanun da ƙyar sosai ta kallesa. Cikin siririyar muryarta data surka da mayen barci ta ce, “Yay..a Mu...sad...diq”.      Jikinsa har rawa yake wajen amsa mata da, “Na'am Samraah! Kandalata nine. Buɗe idonki da ƙyau ki sake ganina. Alhamdullah ya rabbi Alhamdullah.” yanda yake sambatun yana hawaye ga dariya sai ka ɗauka ya zautu ne. Su dai su Mum na tsatstsaye ciko-ciko kawai suna kallonsu. Musaddiq da duk ya gama rikicewa ya zaro wayarsa da sauri. Mansoor ya fara kira, dan abokin kuka shi ake fara gayawa mutuwa, wani ihun farin ciki da Mansoor ɗin ya saki sai da ya janye wayar dan jin zai fasa masa dodon kunne. Daga nan yay kiran d.c.o shima dan ya sani. Shima yanda yake ta jera Alhmdllh zai tabbatar maka yaji farin cikin. Suma yan gwarzo yay kiransu ya sanar musu. Ai kafin kace mi anata shigowa gidan, dan Mansoor ma cikin ruwan nan ya taho duk da gari bai gama washewa ba, sai daga baya jama'ar gidansu suka biyosa. Sanda suka taho an wuce da Samraah asibiti domin duba lafiyarta kamar yanda d.c.o ya bada umarni. Dan sam Samraah bata cikin hayyacinta saboda allurar da sukai mata.......✍️ _Hummm dangin Samraah sai a barmu mu hyaƙata, ga ƴarku nan mun sakar muku. Su o'e duk an addabemu dama🚴🚴😞._ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒕𝒉𝒓𝒆𝒆_ .......Lokacin da goma tayi gidajen rediyo dana tv da yawa sun sanar da ganin Samraah. Gidan tvn su ne ya fara fitar da batun, dan danan sai ga ƴan jarida. Sai dai an hanasu kowace irin dama ta ganin Samraah, dan har lokacin barci ma takeyi ita. Ƴan gidansu ma da ƴan gidan su Mansoor duk suna daga waje ne. Sai wajen sha ɗaya ƴan Gwarzo suka iso suma. Nan fa asibitin ya ƙara cika. Dole doctor ya roƙa su ragu. Dan ana buƙatar sanda zata farko ta farka a cikin hayyacinta. Gamsuwa da hakan yasa aka ragu, Mansoor da Yaya Musaddiq da Abba sai Kawu Musa kawai aka bari, sauran duk suka wuce gida.         Ƙarfe ɗaya da wasu mintuna Samraah ta farka. A lokacin babu kowa a ɗakin dan wanda aka bari asibitin duk sun wuce massalaci salla. Sai Nurse da aka bari ta kula da ita dan zata iya farkawa a koda yaushe. Hakance kuwa ta faru. Sai dai tana buɗe idanunta bakinta da addu'a Nurse ɗin nan ta miƙe. Sannu ta mata da farko, sai kuma ta ɗan fita kamar zatayi kiran Doctor ne. Babu jimawa sai gata ta dawo. A lokacin Samraah ta ɗan daddafa ta tashi dan wani irin fitsari take ji. Matsowa Nurse ɗin tayi gaban gadon tana mai cire wayar dake a kunnenta tai ɗan danne-danne da bai wuce sakan biyar ba ta nuna wayar akan fuskar Samraah dake kallonta. Dan ta rufe fuskarta ruff da face mask idanunta kawai ake iya gani. Baki Samraah ta buɗe zatayi magana da ƙyar dan ganin Nurse ɗin ta saka mata waya a gaban fuska. Amma saita mata nuni da wayar alamar nan zata kalla. Babu musu ta juya kanta a hankali tare da buɗe manyan idanunta da suka kumburo sosai sukayi ɗan ja a jikin fatar amma cikinsu tar-tar ta sauke su akan fuskar wayar. Numfashi ta nema janyo wa da sauri, amma hakan ya gagara sakamakon cin karo da fuskar wanda batai zato ko tsammanin gani ba shima ya zuba mata idanun nan nasa tamkar zai cinyeta ɗanya da su. Zaune yake ƙafa ɗaya kan ɗaya da salon zaman ƙasaitar nan tasa. A yanayin location ɗin da yake zai tabbatar maka da ba'a Nigeria yake ba ma. Duk da ta cikin wayane jinai kallonsa na neman yamutsa min kaina. Amma na dake a zahirance, sai ma wani irin mummunan kallo da nima nake jifansa da shi batare da nasan ina yi ba. Ƙara tsatstsareni yay da idanun cikin yanayin irin ke baki da kunya ko. Niko na yamutse fuska irin eh banda kunyar sai yaya.        Hannunsa ya kai ya shafo gashin dake a haɓarsa, cikin salon ƙara tamke fuskarsa cike da gizago shi a dole bai san raini murya a kausashe ya fara magana da ƙyar dan yanda lips ɗin ma ke motsawa kaɗan-kaɗan sai ka ɗauka bazaka iya jin abinda yake faɗa ba. Amma kuma sai na dinga jin muryar tasa raɗam a kunnena kamar ba'a waya yake ba.     “Ganinki cikin zur'arki bashi ke nufin wasan ya ƙare ba. Sai dai kina da zaɓi biyu. Bakin ki ya kasance shiru ki cigaba da rayuwa da waɗan nan mutane biyun”. Hoton Hafizzullah da Yaya Musaddiq ya bayyana. Bamma san sanda na waro idanuna waje sosai ba ina ɗan zabura. Shiko hankali kwance ya ciga da faɗin, “Ko ki buɗe sa da zance a kaina ni kuma na rufe miki shi ta yanda ko mai irin harafin farkon sunana kika ji sai kin firgita. Na barki lafiya”.        Da sauri nima cikin jin wani ƙarfi na ce, “Yaƙin sunƙuru ai na mai tsoro ne. Idan ka cika namiji kabar laɓe-laɓe a bayan ƙarfin dukiya kazo muyi gaba da gaba sai a banbance waye jarumin tsakanin ni da kai. Ita Sam-G a ko ina Samraah ɗinta take, bana ado da wasu domin kare suna ko ƙarfin iko na. Sannan garkuwa da wasu domin cimma buri ai tsohon salo ne. Video ne dai bazan bayarba, kuma har abada bazaka taɓa sanin inda yake ba, kai ni kaina bazaka sake gani na ba”.         Wani jahilin murmushi ya saki da sai da ƙirjina ya harba dan wani kalar mugun ƙyawunsa ne ya sake bayyana. Idanunsa ya ɗan lumshe da sake buɗewa a kaina cikin yanayin kallon ƙasa-ƙasa, bamma san na murguɗa masa baki da janye nawa ba. Ya ɗan taɓe baki cike da basarwa. Tare da motsa lips ɗinsa a daƙile ya ce, “Ina matuƙar son wasa da mutum irinki mai taurin kai da kaifin baki. Dan haka kar kiyi gaggawa, in dai yaƙin gaba da gaba ne yana tunkaro ki, dan haka jekiyi shiri na musamman, dan yaƙi da Awwab Maash dai-dai yake da tunkarar mayaƙan duniya. Bye sai mun haɗu a filin daga”. Ya ƙare magana da salon kashe ido ɗaya ya ɗaga min yatsu biyu. Ai bamma san na zabura baya ba ina waro idanuna gaba ɗaya waje dan al'ajabi, ka jimin kwarto zai iskantani, dan wannan abun da yay ai na ƴan iska ne. Baki na buɗe zanyi magana. Ɓat ya ɓace tamkar bai taɓa bayyana a fuskar wayar ba. A hargitse na kalla Nurse ɗin da ke ƙoƙarin amshe wayarta. Itama ni take kallo. Cikin tsumar jiki na ce, “Malama sake kiransa!”.      Baki taɗan taɓe, a gadarance ta ce, “Ai shi Boss GIWA ne baya WAIWAYE.”             Cikin ɓacin rai na ce, “Wacece ke?”.     “Sanin wacece ni bazai amfaneki da komai ba. Kare rayuwar ƴan uwanki biyu shine mafi muhimmanci gareki da yin shirin yaƙin dake tunkaroki kamar yanda ya faɗa a yanzu, dan shi baya magana biyu, kada ki sakankance da yawa, in har yace zaiyi, to lallai ya gama shirya yin ne. Idan yace bazai yi ba, babu mai sakasa yin. Zan sake baki shawara akan abinda boss ya faɗa miki. Idan kin kiyaye tabbas kin tsira, domin shi tamkar ifiritin ALJANI yake. A duk inda kika saka ƙafarki yanzu ki ɗauka yana biye dake ne taku bayan taku. Rayuwar ƴan uwanki tana da matukar muhimmanci a gareki, kece kuma zaki tabbatar ma da duniya hakan ta hanyar sakawa a ranki kamar baki taɓa ji ko ganin komai ba akan Boss. Zaɓi ya rage naki, nima na barki lafiya”.      Da sauri na yunƙura da nufin cafkota, sai dai wani irin jiri ya nema kwasata dole na koma saman gadon jagwaf ina mai dafe kaina dake juya mun. Dai-dai nan Doctor ya shigo tare da Nurse. A kaina suka rufu suna jera min sannu. Niko gaba ɗaya ma bawai ina jinsu bane ba da ƙyau. Dan hatta ɗakin jinake yana amsa amon muryarsa tamkar a yanzun ne yake jera min gargaɗin ko barazana zan jirashi ma ban sani ba. Sama-sama nake jiyo doctor na faɗin, “Barcin nan bai gama sakinta ba. Sister Fadila gyara mata kwanciya”. Daga haka ban sake jin su ba.       ★★Sai yamma lis na sake farkawa. Yanzu kam Alhamdullah dan duk wanda ya kalleni yasan ina a hayyacina. Dukan ƴan uwana kuma an basu damar shigowa dubani. Ina zaune a gadon na jingina da filo Gwaggo Gudidi na bani shayi. Gaba ɗaya idona ya kasa barin kan Yaya Musaddiq, kaɗan-kaɗan kuma nakan ce masa ya kira Hafizzullah ya ji yana lafiya. Yanda nake ɗin sai kowa ke ganin kamar ban gama saki bane shiyyasa. Niko ni kaɗai nasan a halin da nake ciki. Wani furuci da Mum ta furta lokacin da ƴan gidan su Mansoor suka zo ya saka ɗakin yin tsit duk aka zuba min ido har ina jin jinina na yamutsawa. A gatsine bayan ta kallan da ga sama har ƙasa lokacin da Gwaggo ke lallaɓani na ƙarasa shan shayi ta furta, “Ai waɗan nan kidnappers ɗin ma dai masu mutunci ne da wayewar kai. Yanda duk wanda aka kama ke dawowa wujiga-wujiga amma ita Samraah gata nan fes da ita. Sai ma uban haske data sake ga fata sai ƙyallin jin daɗi take yi kamar mai yaron ciki. Koda yake ance idan sukaga masu ƙyau musamman ƴammata sukan maida su kamar matansu ne suyita musu gata kuma. Maza ne dai ke shan baƙar wahala da duka. Da alama kema dai sa'ar kika ciwo kansu ɗiyata, mudai in ma wani bai aureki a cikinsu ko ya lalata miki rayuwa ba ai Alhamdullah, duk da kema ɗin ba abin yabo bace tunda dama ko ina yawonki kike yi tumma kan faruwar hakan”. Gwaggo Gudidi ce ta katse shirun ɗakin idonta akan Yaya Musaddiq daya wani dunƙule hannu. Gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun gama fitowa alamar yau ɓacin ran maza ya fito fili. Ya ɗan motsa da alamar zai yunƙuro Gwaggo ta katse hakan ta hanyar duban Mum da ƙyau. Murmushi ta sakar mata itama, sannan ta furta,........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒇𝒐𝒖𝒓_ .......“To banda abinki Jalilah ai kidinafa ɗin dama kala-kala ne. Duk wanda ya fahimci wanda suka ɗauki Samraah kuma ai yasan ba masu neman kuɗi bane. Akwai wata manufa da ake son cimmawa. Ba kuma na raba ɗayan biyu akan rahamar da UBANGIJI yay mata ta samun miji kawai ake son aga an tarwatsa. Sai kuma ALLAH da yake shi maji roƙon bayinsa ne sai gashi ya rusa duk wani makircin masu makirci ƙarfin addu'a yayi tasiri dan gashi UBANGIJI ya dawo da ita gida a lokacin da magauta wannan aure basu so ba. Kuma in sha ALLAHU babu fashi ranar juma'a iyanzu tana nan da igiyoyi uku a kanta”.      Wata irin nannauyar ajiyar zuciya Mansoor ya sauke yana mai lumshe idanunsa. Yayinda Mamyn sa tai ɗan murmushi kawai. Hakama Dad ɗinsa da su Kawu Lurwanu duk murmushin sukayi. Attahir kuwa mintsinin Mansoor yayi yana kashe masa ido ɗaya cike da tsokana. Hakama ƙannensa Islam da Sakeena dake zaune kusa da Samraah duk murmushin sukayi. Aiko Mum kamar zata haɗiyi zuciya, amma dai ta danne tana murmushin yaƙen itama kamar kowa. Abba ma baice komai ba, da ga ƙarshe ya wayance da an kirasa a waya ya fita yana amsawa. Yaya Musaddiq ma a hankali ya dinga sakin ajiyar zuciya jijiyoyin kan nasa na saki sannu-sannu, dan koba komai amsar da Gwaggo ta bama Mum ta fanshi duk wani ɗaci da fushin daya yunƙuro masa. Ni dai kaina a ƙasa ina satar kallon Yaya Musaddiq, zancen Gwaggo ya sakani jin kunyar kowa dake ɗakin musamman ma family ɗin Mansoor. Dan dama tunda suka shigo ban sake yarda na kalli kowa ba. Ko magana da ƙannensa ke mun ƙasa-ƙasa ɗan murmushi kawai nake musu. Lokacin sallar magrib kowa ya watse. Iyayen Mansoor da ƙannensa suka wuce. Hakama Mum da su Kawu Lurwanu Yaya Musaddiq ya tafi kaisu masauki. Shi dama Abba tun wayar nan daya fita bai sake dawowa ba. Su Baby kam har yanzu ban gansu a asibitin ba. Dan ko Abbas dake matsayin babbansu bana jin yama zo dubani, koma basu san na dawo bane oho, koda yake da wuya ace hakan ta kasance gaskiya.     Daga ni sai Gwaggo Gudidi aka bari, sai bayan sallar isha'i ne Yaya Musaddiq da Mansoor suka dawo. Babu jimawa da shigowar tasu sai ga d.c.o da yaransa guda biyu. Sun nuna jin daɗinsu na ganina garau yanzun, dan doctor ma yace zai sallaman da safe tunda banda wata matsala a tare dani, sai rashin ƙarfin jiki na allurar da suka min, tun ma a daren yay niyyar sallamata Mansoor ya ce a barni sai washe gari dai na sake jin ƙarfi da kuzari. Mun gaisa da su suka jajanta min kan abinda ya faru. Kafin d.c.o ya tabbatar min dana kwantar da hankalina na kuma basu haɗin kai mutanen nan ko su waye su sai sun kamasu an hukuntasu.       Amsa masa nai kawai da kaina dan nasan abinda yake faɗar bamai yiwuwa bane ba. Wani ma idan nace ga wanda yay kidnapping ɗina cazai ƙarya nake yi. Su kuwa koda ma sun san gaskiya babu abinda zasu iya yi ɗin kamar yanda yake faɗa. To shi hatsabibin aljanin ma zai basu wata ƙafane da zasu gane shine, dan magana ta ALLAH al'amarin mutumin nan ya fara sakani a firgici, dan bana jin na taɓa cin karo da makirin mutum, hatsabibin gaske da ko tsoro bazaka taɓa karanta a yanayinsa ba irin wannan mutumin. Ga shi yayta wani shan ƙamshi cikin gadara da karfin iko kai kace shike mulkar ƙasar. Ta wani ɓangaren kuma ina buƙatar rayuwar ƴan uwana. Dan wannan mutumin babu shakka zai iya aikata abinda ya faɗa koma fiye da shi tunda na gani da idona sanda yake zare wuƙa a jikin wani. Ga kuma abinda Nurse ɗin nan tace, a duk inda muke yana biye damu ƙafa da ƙafa. Zan kare rayuwar ƴan uwana kamar yanda yay min barazana, sai dai fa idan yasan wata baisan wata ba. Nayi alƙawarin saina ƙullama rayuwarsa tarkon da bazai taɓa iya kuɓutar da kansa ba. Dan saina tabbatar masa da *_TSUTSAR NAMA ITAMA NAMA CE_* da ƴar Abdul-wahab Gwarzo yake magana. Nashi kuma wasa ne, bai san mi ake kira kaidin mata ba sai na tabbatar masa.....        Taɓanin da Yaya Musaddiq yay ya sani dawowa hayyacina firgigit. Cike da kulawa ya furta, “Tunanin mi kike anata magana Samraah?”.     Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi, sai kuma cikin sanyin murya na ce, “Ba komai Yaya. Kuyi haƙuri”.    Baki ya buɗe zai sake magana naga ɗan sandan ya masa alamar ya barni. Shirun kuwa yayi, suma sai sukai mana sallama akan zasu wuce. Amma an ajiye ƴan sanda biyu domin tsarona gudun abinda zaije ya dawo. Godiya Mansoor da Yaya Musaddiq da Gwaggo suketa jera musu, ni dai bance komai ba face zamewa na kwanta kawai. Dan a ganina bani ke buƙatar ƴan sanda ba Yaya Musaddiq da Hafizzullah ne. Tunda idan sake niyyar saceni yay nikam nasan abune mai sauƙi a garesa. Nama fara zargin bayan Nurse likitan ma nasa ne. Kai kowama dake asibitin kallon yana da alaƙa da shi nake yanzu. Sai dai ban san ta yanda zan fito na faɗi hakan ba kuma a fahimta a kuma gaskata ni.....        💢💢💢💢💢💢💢     Agogon dake bangon ɗakin ta sake kallo a karo na barkatai, sai kuma ta ja sirrin tsaki. Ɗagowa mijin nata yay ya kalleta. Ganin yanda ta ɗauke kai gefe ya sashi faɗin, “Lafiya kuwa kike Safina?”.     Kanta ta ɗan girgiza, cikin nuna damuwa ta ce, “Ba komai. Yaron nan ne dai al'amarinsa ya fara bani tsoro. Kalla agogo maganar ɗaya ake na dare amma har yanzu bai shigo gidan nan ba. Hakan na nufin a asibitin zai kwana ko mi?”.        Agogon ya kalla shima, sai kuma ya ɗauka wayarsa batare da yace mata komai ba. Kunnensa ya kai alamar kira yake bayan yay ƴan danne-danne. Ana ɗagawa kuwa bayan amsa sallama ya ce, “Ɗan uwanka bai dawo gidan nan bane har yanzu Attahiru?”. Ɗan jimm yay alamar saurare. Sai kuma ya janye wayar batare da ya sake cewa komai ba. Kallonsa Mamy tayi cikin ƙagara ta ce, “Bai dawo ba ko?”. Kansa ya jinjina mata alamar eh. Zai cigaba da aikinsa a computer ta dakatar da shi. “Ya kuma zaka cigaba da aiki ka dadynsu? Ka kirashi ɗan ALLAH mana muji yana ina”. Kafeta yay da ido na tsawon sakanni. Sai kuma ya girgiza kansa da faɗin, “Mansoor yaro ne ƙarami Safina. Karki manta shirin ɗaura masa aure fa ake nan da kwanaki huɗu. Kinga ko ai yasan abinda yake ko”.         “Nifa gaskiya Daddynsu bana wani jin batun auren nan a raina yanzu. Kuma dama can kaima kasan dan ya nace ne akan yarinyar nan yasa ka zuba ido da kuma dagewa da nayi nima saboda yarinyar ta shiga raina da farko. Amma magana ta gaskiya maganar matar kawunta ta ɗazun ta shigeni matuƙa. Shiyyasa tunda na dawo gidan nan naketa auna abubuwa. Dan zancen abin a duba ne fa, musamman idan muka tsaida hankalinmu muka nazarci komai a yanda yake”.       Idanu kawai ya zuba mata kamar zai cinyeta da su. Itako ta ɗauke kai tana wani kum-kum da fuska tabbacin zancen nata fa tun daga zuciya ne.      “Safina kin san kuwa mi kike faɗa? Kin san fa yanda ɗanki ke matuƙar son yarinyar nan. Idan har a baya na kasa hanashi dake kanki a yanzu mi kike tunanin zan iya? Naga kece kika zaƙe da faɗar ƙyawawan halayyar yarinyar a baya duk da ni na nuna batai min ba. Ina baki shawarar kawai ki bisu da addu'a kamar yanda kika saba tun farko. Maganar matar kawunta kuma ai ba lallai ne ya zama gaskiya ba. Tunda ba'a san wani kalar kidnappers ne suka kamata ba.....”       “Oh amma yallaɓai su Kidnappers ɗin har suna da wani banbanci da juna ne?. Ai duk wanda akace kidnapper to Kidnapper ɗinne kawai babu wani ba rabe a ciki. Na kula yanzu ba gane maganata kake ba, bayan kuma ada ba son yarinyar kake ba, ban san miya canjaka a yanzu ba kuma. Amma dai ka zauna kayi nazari kaima. Wlhy sam babu alamar wahala a tattare da yarinyar nan. Sai ma uban haske da ƙyau data ƙara duk da kuwa sau biyu na taɓa ganinta ido da ido. Amma ai biye nake da program ɗinta duk sati a gidan tvn su.”          Shi kam dai Dad ɗin su Mansoor yama kasa magana. Dan mamaki ma da al'ajabi matar tasa ke bashi yau kam. Sai yake ganin kamar ma ba ita ba. Irin wannan kafiya haka har ina kuma. Anya kuwa ba wani ne ya zugata ba?. Bashi da mai bashi amsa. Dan haka ya girgiza kansa kawai yana ƙoƙarin manyan abubuwan dake ransa tare da haɗiyesu a zuciyarsa da ga shi sai UBANGIJINSA. Gudun damuwarta saboda tanada hawan jini ya sashi sassauta nasa yanayin, cike da kulawa ya ce, “Tom naji zanyi nazari kamar yanda kika ce in sha ALLAH. Kuma zan yi bincike. Shima ɗan naki bari na taɓasa a waya. Ki kwanta ki huta kema”. Kafin ma tace wani abu ya ɗauka wayarsa ya fara ƙoƙarin kiran Mansoor........✍️        _Tofa wata sabuwa masu karatu🥱_ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒇𝒊𝒗𝒆_ ......Yana kai wayar kunnensa dai-dai nan ma yake jin horn ɗin motar Mansoor ɗin da ƙarar buɗe gate. Wayar ya sauke tare da ajiyar zuciya ya ce, “To Alhamdullah gashi can ma ya dawo ai. Sai ki kwantar da hankalinki      Ajiyar zuciya Mamy ta sauke kuwa. Ta yunƙura zata miƙe Dad ɗin ya zuba mata ido. “Ina kuma zaki?”. “Zanje na duba shi ne mana. Kofa abincin dare baici ba. Kasanshi kuma da abinci, inba tsaresa akai ba ba wani son ci yake ba”.     Kai Dad ɗin ya girgiza. Sai kuma ya ce, “Uhm kinga Safina zauna Please”. Babu musu ta koma ta zauna. Sake cemata yay “Kwanta sai da safe. Tunda dai Mansoor ba jariri bane balle kice baki gama rainonsa ba.” tasan halin mijin nata dan haka bata sake magana ba kuma. Sai dai zuciyarta gaba ɗaya tana akan son sanin a wane hali ɗan nata yake ciki. Amma tunda yace bazata je ba to bata isa fitarba kuwa. Shima dai hankalinsa ya sake maidawa ga aikinsa bai sake bi takanta ba kuma. Ga shi ya haɗe fuska dan bama ya son tace zata roƙesa ko ta takura masa da batun auren Mansoor ɗin kuma.....                  💞🌟💞🌟💞🌟💞     Washe gari kamar yanda doctor ya faɗa aka sallameni. Gwaggo Gudidi taso wucewa da ni can Dawanau gidanta amma Yaya Musaddiq ya roƙeta kan ta barni na koma can gidan ɗin. Tunda har Mansoor yayi magana kan baya son a ɗaga bikin nan a yanda yake koda na kwana ɗaya ne kawai ayi a wuce wajen. Ya kamata kuma muje can gidan Abba a ƙarasa komai daya kamata kada halin Mum ya dameta. Badan Gwaggo taso hakan ba ta yarda.         Tarba muka samu babu yabo babu fallasa da ga Mum. Hakama su Baby na zaune a falo amma babu wanda yay min sannu ko nuna farin cikin dawowata garesu. Sai auta ne ya tsillo da gudu ya ruƙunƙumeni. Duk da miskilancin yaron sai da ya furta, “Adda nayi kewarki. Adda Bibaa tace kin mutu bayan sake ganinki ba ashe ƙarya take min”.     Murmushi kawai na masa tare da shafa fuskarsa. Yayinda Gwaggo ta riƙe haɓa da faɗin, “Ta mutu kuma? To in ALLAH ya yarda ba yanzu ba, mu bazamuga mutuwa ba sai alkairi nan da kwana huɗu. Ke kuma baƙin halin naki sak na uwarki dai ashe, da wani shegen goshinki kamar jirgin tsallake ruwan bagwai”. Ta ƙare maganar tana nuna Bibaa data tura baki gaba zomomo. Na zata Mum zatayi magana. Sai naji shiru ta dai sake tsuke fuska. Ni dai sai ma na yunƙura na nufi bedroom ɗinmu dan so nake na ɗan watsa ruwa ko zanji daɗin jikina. Yanda na tadda ɗakin kaca-kaca sai da ƙirjina ya buga. Abu sai kace turken dabbobi. Wai ni yaushe Bibaa zatayi hankali ni Samraah. Na jima tsaye zuciyata cike da takaici ga ƙyanƙyami dan bazan iya zama a ɗakin ba. Dole na juya na fita cikin ƙarfin hali da son ƙarfafa kaina. Har yanzu duk suna a falon, Gwaggo Gudidi tai saurin faɗin, “Ya kuma kika fito Samraatu lafiya dai ko?”.         Kaina na jinjina mata a yanayin rashin ƙarfi jiki, cikin yamutse fuska na ce, “Gwaggo zan ɗakko kayan shara ne ɗakin yayi datti ina jin ƙyanƙyami”.     Dukansu sai da suka ɗago suka kalleni. Yayinda Gwaggo ta riƙe haɓa da faɗin, “To kaji kuma wani sheɗancin kuma, yanzu duk waɗan nan zagada-zagadan ƴan matan uwa wa ƴan matan amarya a gida ashe hotiho suke. Yo ni dama tunda na shigo naga gidan yamun wani harmutsai a ido nasan ana ƙwaɓa hauka dan har bashi-bashi da tsami-tsamin dauɗa nake shaƙowa ma. Yanzu ke Julaila kike ko mima oho miki bayan koyama ƴaƴanki rashin kunya abinda zai taimaki rayuwar tasu ma kin tauyesu basu iya ba. Komai kun tattara akan marainiyar ALLAH. To wlhy ba mugunta kikai mata ba idan ma ke haka kike tunani, su waɗan nan da kike gani ƴan hutu a gabanki su kika kashewa rayuwa, dan su zasu gurji kan ubansu nan gaba kaɗan. Zaku ma ki tabbatar da hakan ke da su ranar da tusa ta ƙarewa bodari, ɗiya mace bata iya komai ba ai bata cika mace ba wlhy, babu kuma namijin da zai juri zama da ita, idan ma ya haƙura ya jure dan yanada kuɗin biyan wasu suyi to bazata taɓa daraja a idonsa ba dan wataran ko shine ƙaruna akan kuɗi zai so matarsa ta masa hidima. Kai ai wlhy baki birgeba kuwa. Ashe ma fuggukar taki da ɗaga hanci kamar ƙofar gora na wofine” ta ƙare faɗa a fusace. Bibaa ta nuna da Baby “Ku dan ubanku Imamu ku tashi ku ɗakko kayan shara, ke kuma zoki zauna anan wazai barki kiyi wani aiki kina fama da kanki. Zakiyya ma na hanya gyaran jiki zata fara miki yau ɗin nan dan duk da gaki nan fes da ke ga kuma ƙarancin lokaci bazai hana nasa a kwaskware min ke ba dan kowa ya sake tabbatar da amarya ƴar gata zan kai”.       Sosai Bibaa da Baby ke kallonta ransu a ɓace, sai kuma su kalla Mum da taƙi cewa komai. Tsawa ta daka musu, babu shiri suka miƙe a zabure kuwa. Nayi mamakin shirun Mum dan nasan yanda suke ƴar tsama da Gwaggo Gudidi, rashin jituwar tasu ma ce tasa Gwaggon daina zuwa gidan gaba ɗaya. Amma dai dole a wannan shirun nata akwai ayar tambaya.      Su Baby naji na gani Gwaggo ta turkesu sukai gyaran ɗakin, sau biyu tana maidasu su maimaita wai bai mata ba. Bayan sun kammala sunata zungure-zunguren baki tasa Bibaa ta tattara kayanta ta maida ɗakin Baby. Shima auta aka haɗa masa nasa aka sanda shi ɗakin Mum. Acewar Gwaggo nan sune zasu zauna har sai biki ya tashi. Ni dai dariya ma abin ke ban. Dan Gwaggo Gudidi fitinanniya ce sai dai idan bataso ba zaka ga ta watsar da kai kamar mai shiru-shiru. Halin namu dai na kamanceceniya sosai, ƙila dai ita na gado ma (🤣). Fuu Mum ta tashi batare da tace mana komai ba ta bar falon, mu duka da kallo muka bita, sai dai babu wanda yace komai. “Mum na shiga ɗaki waya ta ɗauka, sai faman huci take da jan numfashi, kai daka ganta kasan dama danne komai take da ƙyar kawai. Ko sallama balle gaisuwa batayi ga wanda ta kira ɗin ba ta fara magana a hasale. “Mama magana ta gaskiya bazan iya haƙurin da kikace da wannan tsohuwar ba. Kinga daga dawowarsu yanzu tabi ta addabar min yara. Nidai bazan iya ɗauka ba. Wannan plan ɗin naki na fara jin kamar bazan iya juresa ba. Ina dalili yara tun suna ƙanana sun tare min komai yanzu kuma an saka min ƴaƴa a gaba duk da kwacen saurayi da akaima Baby”. Siririyar dariya akayi mai sauti daga can. Sai kuma dattijuwar murya ta fara faɗin, “Jalila wani lokacin idan kina wani shashancin sai nake ganin kamar bani ce na haifeki ba. Ke matsalarki baki iya ɓoye abu aranki. Shiyyasa tun farko ko riƙon yaran nan nace ki yi na siyasa ta yanda koshi mijin naki bazai fahimci baki ƙaunarsu ko son zama daku ba. Amma ina kin kasa. Yanzu kina ganin matsala ta taso kaso biyu bisa uku na mutane har yanzu ke suke zargi da satar yarinyar nan har da ƴaƴanki. Ko ƴan sandan nan idonsu kema na'a kanki. Amma kin kasa fahimta. Ko shi mijin naki badan mun danne masa kai ba tuni kina ganin bake zai zarga ba ne? Shin wai rayuwa babu siyasa ta yiyu haka ne?”. “Wai Mama sai kice siyasa, siyasa. Dan kawai ina son na birge wani sai na dinga nunawa wanda bana so so. Nidai a bar wannan maganar, kawai ki faɗa min abinda zanyi na gaba dan na fara ƙosawa da halin tsohuwarnan, zan karta mata rashin mutunci wlhy bazata zo cikin gidana ta hanani rawar gaban hantsi ba”. “A'a ban aikeki ba nikam. Ki bari anjima kaɗan zan zo gidan. Dama ga ƴar uwarki nan tazo itama babu jimawa. Kuma ni abinda nasa a raina kofa auren nan akai sai munyi duk yanda zamuyi basu zauna lafiya ba. Dan yanda ta rabashi da takwarata itama bazata taɓa jin daɗin ba. Na fara ji kuma a raina wannan tsohuwar duk itace ke ƙulla komai, maybe ma itace ta amaso asirin da aka juya kan yaron nan. Shiyyasa sam ban sonta tun aurenki da Imam. Amma idan sun san wata su basu san wata ba ai. Daga su har ita zasu ci ubansu ne da ni suke zancen. Yanzu dai ki cigaba da kwantar da hankalinki bana son jin wata fitina. Bari na ƙarasa aiki mu fito”. “To Mama dan ALLAH kuyi sauri”. Suna ajiye wayar zama tai jagwab a bakin gado, ita kaɗai tasan irin ƙunar da take ji a ranta game da auren nan. Ji take kamar ta sakama yarinyar nan shinkafar ɓera a abinci ta mutu kowa ya huta, dan tafi sauran ƴan uwanta tsaya mata a rai, shegiya ga ƙyawu kamar wadda ta tashi a rayuwar hutu, duk baƙar izayar da take mata kullum zaka ganta fes-fes ga shegen Musaddiq ɗin can kullum cikin saya mata suturu yake. Tanada plans daban-daban da zata iya bi ta wargaza auren nan dama rayuwar yarinyar nan duka, amma Mamanta na hanata. Amma yau kam tana ji in har Mama bata iya tayi komai ba itafa zatabi ɗaya daga cikin plans ɗinta ne. Dan bazata taɓa yarda a ƙwacema ƴarta da tafi so abinda ke nata ba. Sai dai ko duk su rasa, ko kuma ƴarta ta samu ita.......✍️ _Humm Mom to bari muga yaya wasan zai kaya 🚴_.      _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒔𝒊𝒙_ .......Bayan nayi wanka nayi sallar Azhar da tayi ina zaune ina ɗan tsakurar abinci zuciyata fal tunani. Zantukan mutumin nan kawai ke min kai-kawo a rai. Dan tun jiya nake son fassarasu amma na gagara hakan. Ina son na sanar ma Mansoor da Yaya Musaddiq gaskiya amma ina jin shakkun abinda zai je ya dawo. In har zai iya saceni harna tsahon kwanaki goma sha bakwai, kuma ya dawo dani gida batare da wani ya gani ko yaji ko gano shine ba har jami'an tsaro wane makami kuke tunanin zan iya ɗauka domin kare kaina?. Bily ina da taurin kai da kafiya. A wasu lokutan harda tsiwa ma. Amma fa babban weakness ɗina a rayuwa sune ƴan uwana guda biyu. Zan iya bada rayuwata a wajen karesu kamar yanda nasan suma zasu iya hakan. Dan su ɗin garkuwa ta ne. In dai hakane kenan ya kamata na kwantar da hankalina na nutsu waje guda har a gama bikin nan na koma ƙarƙashin ikon Mansoor. Na tabbata zai taimaka min da duk irin gudunmawar da nake buƙata game da bama ƴan uwana garkuwa batare da hatsabibin ya farga ba. Na kuma tona asirin sa ta hanyar da bai zato ba. Tunda yanada wayo shima ya kamata a tabbatar masa da TSUNTSU mai WAYO ta baki ake kamasa. Hakan kuma bazai yiwu ba har sai na nutsar da hankalina waje ɗaya na shirya nima tsaf ta yanda zan zame masa tamkar kifin tarwaɗa da baza'a taɓa iya kamashi da santsin kalkashi a hannu ba. Dan a yanzu ni kaɗai nasan inda video ɗin yake. Dan abinda Mansoor bai sani ba ni da kaina na goge na wayarsa, badan kuma ban yarda da shi nai hakan ba. A'a ina tsoron a masa barazana dani ne a amsa wataran. Shiko Yaya Musaddiq dama bai tura ba kwata-kwata. Dan haka na ciresa daga tawa wayar nima na maidashi a flash drive dana sayo na adanashi inda daga UBANGIJINA sai ni muka san inda yake.....        “Oh Amarsu irin wannan zurfin tunani haka?”.    Aunty Zakiyyar Gwaggo da bamma san lokacin data shigo ba ta faɗa cikin katseni ta hanyar taɓani na kawo nannauyan numfashi. “Har kin fara tunanin rabuwa da gidan ne raguwa? Sai bakin tsiya kuma”. Ta sake faɗa cike da tsokana. Murmushi na sakar mata ina duƙar da kaina. Na ce, “Kai aunty yaushe kika shigo bamma sani ba”.      “A taya zaki sani kin lula duniyar tunani. Yaya jikin naki dai to?”.     “Alhamdullah Aunty, dama babu inda ke min ciwo, allurar da suka min ce kawai ta sakani wannan dogon barcin”.          “ALLAH sarki to Alhamdullah ai haka akeso. ALLAH kuma ya kiyaye gaba. Ya tona asirin duk wanda keda hannu a kan hakan. Damma dai Alhamdullah addu'a tayi tasiri ƙwarai da gaske. Kuma da alama duk ma wanda suka kamakin ba mugaye bane. Dan masu amsar kuɗin nan sunfi haɗari. Amma waɗan nan da alama suna da tasu manufar ne a kanki gaskiya. Na kuma fi ƙyautata zaton akan auren nan ne kamar yanda kowa ke zargi, musamman akan wannan maman taku da Baby. Kowa yafi dangantasu da al'amarin nan wlhy, dan zuciyarsu babu ƙyau komai zasu iya aikatawa tunda sun gagara ɓoye hassadarsu”.      “In sha ALLAHU Aunty bazasu ci nasara ba kuma. Tunda gashi ma ALLAH ya kuɓutar dani cikin sauƙi, dan tabbas addu'ar ce tai tasiri a kansu suka sakeni batare da sun shirya ba, amma kuma ni bana danganta al'amarin da su Mum da dalalin auren nan kamar yanda kowa ke kallo, dan in dan auren ne ai kinga babu yanda za'ai su sakeni haka da sauƙi da sai lokacin bikin ya wuce ko”.      “Tabbas hakanne kam Samraah kema kinzo da batun dubawa. Amma dai ai zaki iya ganesu? Dan naga angon nan naki da gaske ya shirya ɗaukar mataki, a yanzu haka suna ƙofar gida da ƴan sanda da Musaddiq da Yaya Imam.”     Idanu na zuba mata kawai, sai kuma na nisa a hankali na ce, “Aunty bazan iya gane su ba. Saboda abinci kawai suke kawo min sau uku a rana. Kuma komai nasu a rufe hatta da hannayensu ma. Kuma basa mun magana sai dai su ajiye kawai su juya su fita. Ko'a ranar dana samu damar kiran Yaya Musaddiq ma kwato nayi, sai kuma suka kamani bayan sun amshe wayar suka shaƙamin abu suka ɗaukeni da ga gidan sai farkawa nai na ganni a wani sabon waje. Hakama yanzu sai da suka min allura sannan suka kawo ni ƙofar gidan nan.”     Aunty Zakiyya na shirin yin magana dai-dai nan Yaya Musaddiq yay sallama. A tare muka amsa masa. Batare da ya shigo ba yace nazo. Miƙewa nai na ɗauki hujjab ɗina na saka sannan na fita. A falon baƙi na samesu shi da d.c.o da Mansoor sai Gwaggo Gudidi da Abba. Daga can gefe Baby ce ta masifar zubama Mansoor ido kamar zata cinyesa. Shiko sai wani cin magani yake tamkar an aiko masa saƙon mutuwa. Sai da muka haɗa ido ya ɗan sauke numfashi tare da sakar min murmushi. Murtani na mayar masa nima ina duƙar da kaina ƙasa. Gaisar da d.c.o nayi cikin girmamawa, shima ya amsa min da kulawa tare da tambayata ya jikina. Kaina a ƙasan na ce, “Alhamdullah bana jin ciwon komai Sir”.       “Masha ALLAH, Alhamdullah haka muke son ji ai dama. Samraah wannan zuwan naki ne. Muna fatan zamu samu haɗin kai domin son sanin komai daya faru dake tun daga fitarki a gida a waccan ranar har zuwa yau da ALLAH ya maido mana ke bisa ƙarfin ikonsa”.        Babu musu na jinjina masa kaina tare da faɗin, “In sha ALLAHU ranka ya daɗe zan faɗi abinda na sani”.      Zamansa ya gayara sosai yana fuskantata. Kafin ya furta, “Yauwa Ina jinki”. Bayani na fara masa tiryan-tiryan tun daga shirin fitata. Kiran dana samu daga MD har zuwa fita cikin layi da tare napep. Jefamin handkerchief da wanda na samu a napep ɗin yayi bayan ya kira sunana tabbacin ya sanni ko yana son tabbatar da ni ɗin ce, har zuwa buɗe ido na ganni a wani waje daban. Yanda na rayu a gidan farko har zuwa kiran wayar Yaya Musaddiq da nayi da wayar ɗaya daga cikin mutanen da kuma canja min gida da sukayi. Sai dai na samu kaina da kasa faɗar wanda ya saka akai kidnapping ɗin nawa kamar yanda ya nuna min kansa da buƙatar na bashi abinda ke a hannuna da yayi, hakama dalilin ɗaukar tawa duk ban faɗa ba. Maidoni gida da sukayi da kuma kiran da yayma Nurse a asibiti ta bani. Kawai dai na sanar musu kamar yanda na sanarma Aunty Zakiyya ne. Sosai falon yay tsitt suna saurarena. Yayinda d.c.o ya kafeni da idanu ko ƙyaftawa bayayi. Jinai duk na tsargu, amma na dake abina kun dai san mutuniyar taku ai. Dan kansa ya gaji ya janye idanunsa a kaina. Cikin sauke numfashi ya furta, “Kin tabbata iya abinda ta faru kenan Samraah? Dan bana son ki ɓoye mana komai, kar kiji tsoron barazana ma idan sun miki babu abinda zai faru”.       “Iyakarsa kenan yallaɓai. In har na ba mance wani abu to bashi da muhimmanci ne”.     Kansa ya jinjina cikin nuna gamsuwa, kafin ya kalla yaronsa dake rubuta duk abinda nake faɗa, sai kuma ya maida idonsa kansu Yaya Musaddiq. “Inaga fa dole ne mu sake gayyatar MD ɗin nan nasu, dan komai idan aka tattara ya ta'allaka ne akansa. Amma bawai ina tabbatar da shi ɗin ne ba. Dan ita shiri'a saɓanin hankali. Kuma tunda har ta dawo gida cikin ƙoshin lafiya Alhmdllh, koma minene zai zo mana da sauƙi. Yanzu dai inaga sai a kiyaye gaskiya. Fita anyhow dole ta jingine ta. Mukuma duk inda ta saka ƙafa idan ma har ta fitan zata kasance a ƙarƙashin kulawarmu ne.”         “In sha ALLAHU babu damuwa ranka ya daɗe. Dan ko batun zuwa aiki ma dama zata ɗan dakata, in ma zata cigaban ne sai bayan bikinta idan mijinta ya amince sai taje ɗin”.     “Wannan ma dabara ce kam mai ƙyau sosai. Amma taron bikin nan fa dole ayisa da kulawa. Koda yake zamu haɗata da jami'ar mu mace domin ta kasance da ita ama duk inda take like handbag ɗinsu na mata. Hakan zai sauƙaƙa mana aikin mu insha ALLAHU.”      Kowa a falon yaji daɗin zancen nasa kuwa. Dan har fuskokinsu sun gagara ɓoyewa. Ni dai kaina a ƙasa kawai abubuwa da yawa nata min kai kawo a zuciya. D.c.o ya ɗan ƙara tattaunawa da su Yaya Musaddiq kafin suyi mana sallama su wuce. Tare da jaddada min duk sanda suka buƙaci gani na zan iya ganinsu a gidan, ko kuma su aiko a ɗaukan zuwa office ɗinsu. Da to kawai na amsa musu ni dai. Gwaggo Gudidi sai jera musu godiya take. Mansoor da Yaya Musaddiq kuma suka tafi musu rakkiya waje. Muma miƙewa mukai muka koma cikin gidan. Dan Aunty Zakiyya ta tabbatar min da yau babu fashi zata fara min gyaran jiki. Ban musa ba, dan nima ina son zuwa fadar masoyina fes tamkar wata ɗan daren sha biyar.........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒔𝒆𝒗𝒆𝒏_ ........Tun daga shigowar ƴan sanda har fitarsu a gidan Mum ta sani, amma batako leƙo ba. Sun tafi ma babu jimawa sai ga Mamanta da ƙanwarta dake aure a Bauchi. Acewarta tazo ne bikin Samraah domin yima Mom Kara. Bata bari sun zauna a falo ba ta shige dasu bedroom ɗinta. Da kanta kuma ta fito ta haɗa musu abinci takai musu. Ko kunya babu yanda ƙanwarta ta cire mayafi ta fara lodar abinci haka itama Maman tayi. Kai bakace a gidan suruki take ba. Bayani ta sake ma ƙanwar tata akan duk yanda aka samo Samraah, dan ita Mamansu tasan komai. Ƴar uwar tata kai ta jinjina. Sai kuma tai ɗan jimm alamar tunani, kafin ta sake ɗagowa tana kallonsu bayan ta gama ƙulla abinda take ganin zai fanshi yarinyar nan tsakaninta da ALLAH. Dan magana ta gaskiya ita su Samraah sun jima suna bata tausayi, sai dai bazata iya fitowa ta faɗa ba dan tana shakkar Yayar tata da Mamansu saboda masifaffu ne na bugawa a jarida. Amma tana ji a ranta a wannan gaɓar bazata bari a cutama marainiyar ALLAH ba. Sai dai dole tai komai cikin siyasa. “Niko inada shawara”. Ta faɗa kanta tsaye.duk sake maida hankali sukai a kanta. Cike da zumuɗi Mum tace, “Miye shawarar Ikili, dan ALLAH faɗi muji”. Numfashi Ikilima ta sauke tare da ajiye cokalin hannunta ta sake fuskantarsu. “Ban sani ba shawarar ko zata gamsar daku, amma dai a yanayin da nake gani kamar guri ya ƙure mana a yanzu zata iya zama mafita. Mizai hana mubar yarinyar nan tai aurenta kawai. Bayan bikin mu duƙufa samowa Baby mijin aure na garari da yafi shi wannan yaron. Bayan itama ansha nata bikin mun nunama musu koda goma ta lalace tafi biyar albarka, sannan mu fara shiri akan komai ma da muke ganin ya dace akan auren nata. Dalilina na kawo wannan shawarar shine idan fa muka hana auren nan kamar mun gogama gidan nan wani baƙin fenti ne. Kun san dai halin mutane ai, hakan kuma na nufin kammu muka cutar tunda namu yaran ne dai basuyi aure ba a bayanta, dan ita wani zai iya jin tausayinta yazo ya aureta, sannan mu za'aita zagi da zargin mun hana ko muna mata baƙin ciki. Amma idan muka bari akayi hankali kwance babu mai aibanta mu balle idan mutanen kirki sun zo neman auren su Bibaa wani shege ya sokemu. Kunga mun samu nasara biyu kenan, mun kuɓutar da yaranmu, sannan mun sama musu abinda muke fata. Yo har miye wani Mansoor yake ma komi ALLAH na tuba. Shi da dukiyar ba tasa bace ta babansa ce. Mu ɗan gaske zamu samo mai dukiyar kansa da kansa. Dama ba akwai mutumin nan daya haukace akan baby na anguwarmu ba amma tanata masa wulaƙanci ita bazata zauna da kishiya ba. To wlhy yanzu yazo nan Kano yayi wani mahaukacin gida a hotoro g.r.a ina gaya muku kuma aure yake son yi ruwa a jallo ya saka matar anan, su kuma waɗan can zasu cigaba da zamansu can Bauchin saboda ya musu tayi sunce su bazasu iya barin mahaifarsu da ƴan uwansu ba. Amma yaya kuka gani?”. Cike da zumuɗi Maman ta ce, “Ni dai wannan shawara tamun wlhy Ikilima, amma ke Jalilah yaya kika gani?”. Shiru Mun tai kamar bazatace komai ba, sai kuma ta sauke numfashi mai nauyi da faɗin, “Nima shawarar ta ɗan mun, sai dai ina tsoron tsutsun Baby wlhy, Dan nasan yanda ta tsani kishiya...” “Yo biye mata zamuyi, tuni zamu shiga mu fita a dasa mata sonshi a zuciya sanda ma zata soshin fawa tai shawara. Mufa muka haifeta ba itace ta haifemu ba. Kishiyoyi kuwa ai dasu da babu duk ɗaya ne tunda ba'a waje guda zasu zauna ba”. “Yo Mama ko waje guna ne Baby bata da matsala. Dan matansa wlhy a hakan ma kowa rayuwarsa yake babu wadda ta damu da wata tunda kowa da gidanta kuma kowacce kuɗi take juyawa na hauka. Yi kishin ma fa dama matan malam shehune sukafi zaman yin na haukannan aita damben tsiya da hayaniya. Amma mata masu aji da kuɗin nan zakiga kishin ma na ƴan boko akeyi, itama kuma dai tanada iliminta babu abinda za'a nuna mata. Kuma tana shiga zai bata maƙudan kuɗi ta fara kasuwanci kamar sauran dan haka yake yi” “Hakane wlhy Ikilima. Ni kubar komai a hannuna kawai zanyi maganinta, yanzun kam hidimar biki duk mu ware aitayinta damu. Ai kwantan mage zamu musu a yayin kama ɓera, tuni sai suzo hannunmu batare da sun farga ba”.... (😂ALLAH ya rabamu da son zuciya to). 💦🌟💦🌟💦🌟💦 Zaune yake a office yana ƴan ayyukansa sakatariyarsa ta shigo ta sanar masa d.c.o yazo yana son ganinsa. Karo na farko da MD yaji ransa ya fara ɓaci da bibbinin da d.c.o ɗin ke masa. Idan yace da yana da dalili yanzu kam shi baiga dalilin ba. Samraah dai ce ta kuma dawo sai me kuma, shi ma yaje dubata tare da staffs nasu har asibiti. To minene kuma na zuwa masa office yau. Rashin amsa ya sashi jan sirrin tsaki, tare da bama sakatariya umarnin ta barsa ya shigo.     Fitarta bai fi da mintuna uku ba ko sai ga d.c.o ɗin ya shigo, sun gaisa cike da girmama juna. Kafin MD ya ce, “Yallaɓai akwai wata matsala ne?”.     “No babu matsalar komai MD. Waccan dai matsalar ce akan staff ɗinku Samraah Abdul-wahab Gwarzo. Dan kasan koda ta bayyana ya kamata mu cigaba da bibiyar case ɗin domin gano da kama wanda sukai kidnapping ɗinta kodan musan dalilinsu”.            “Hakan nada ƙyau yallaɓai. Domin muma zamu so ace an kama sun. Sai dai muna ƙarama ALLAH godiya da kuɓutar tata cikin ƙoshin lafiya. Yanzu mike tafe da kai?”.       “Uhm kamar dai yanda aka saba zamu sake gayyatarka office ɗin mu idan babu damuwa. Kana kuma da damar muje ka samemu a can, ko mu tafi tare”.      Murmushi MD yayi mai ƙayatarwa. Sai kuma cikin rashin damuwa ya ce, “Babu matsala muje ɗin kawai, dan bawani aiki nake da shi ba sosai yanzun. Zuwa anjima kuma aikin zai iya shamin kai, kaga kuma bai ƙyautu ace ban amsa gayyatar ba”             “To Masha ALLAH, hakane kam mun gode sosai”.     Murmushi kawai MD ya sake masa yana miƙewa. A jere suka fice suna ƴar hirarsu tamkar wasu abokai. Dan haka sauran staffs basu fahimci komai ba face tunanin akan dai case ɗin Samraah ɗin ne. Kuma babu wani damuwa a cikin ganin MD da ƴan sandan dake bincike akan case ɗin tunda ba yau ne mafari ba. Suma kansu dai duk sai da suka sha tambayoyi a kwanakin baya....        💢🌟💢🌟💢🌟💢   Kwanaki na biyu kenan da dawowa gida. Kwanaki biyu kuma kacal ya rage ɗaurin aurena. Dan zuwa yau har baƙin kusa sun fara isowa musamman dangi na jiki sosai. Ga Aunty Zakiyya ta duƙufa min gyaran jiki da ɗuramin abubuwa. Niko dana faki idonta sai na zubar dan bana sha sosai. Abinda zai baku mamaki duk da haramin biki da gida ya fara ɗauka ga masu gidan babu wani alamar motsi irin na biki a tattare da su. Dan hatta da abinci da aka girkama baƙin dake a gidan yau Yaya Musaddiq ne ya kawosa. Suko su Gwaggo suka girka batare da sun bi takan Mum daketa faman ɗacin rai ba. Shi dai Abba saboda su Gwaggo Gudidi yana ɗan nuna alamar damuwa da shirye-shirye. Sai dai fa bana aljihu ba na gayyatar mutanensa kawai, sai kuma takurama Yaya Musaddiq da yake ta bayan fage akan kuɗin kayan ɗakina da wanda za'ai hidimar abincin biki. Shiko Yaya Musaddiq nata masa zame-zame. Sai a yau ya fito fili ya shaida masa karya damu shi ya riga da ya kammala komai. Dan hatta da kayan kitchen ɗina ma a tanade suke tuni. Hakama kayan gado kafintan ya jima da kammalasu duk da Mansoor yace kar ayi shi baibi ta nasa ba. Wannan zance ya ƙona zuciyar Abba matuƙa. Amma ya gagara magana kodan mutane dake cike a gidan, yasan fitowar zancen babban abin kunya ne a garesa musamman a wajen danginsu dana ɓangaren mahaifinmu.           Ban gayyaci wasu ƙawaye ba dan banda su, amma a ranar da yamma sai ga su Ruƙayya ƴan Office dinmu da gayyar ƴan ajinmu na islamiyya. Naji daɗin ganinsu sosai, dan ko kusa banyi zato ba. A bakinsu na fara jin ƙananun maganganu akan rashin kawo kayan da zanyi amfani dasu na biki da Mansoor ya ce sai daga baya dan ba'a saka ɗinkakken kaya ko ɗaya a lefen ba, kuma kowa na saka ran yau ne za'a kawo ɗin saboda kamu da ake shirin yi gashi babu kayan dazan saka. Amma har yamma shiru kake ji. Gashi yanzu banda waya a hannuna ko ɗaya. Rabona da Mansoor kuma tun jiya da dare. Koda yake nice nace yau kar yazo, kai daga jiya ma bazan sake yarda mu haɗu ba sai a gidansa. Shiko ya yarda da hakan acewarsa zai gwada yaga ko zai iya. Nayi tunanin kiranshi amma zuciyata ya ƙwaɓeni game da hakan, dan haka bance da su komai ba na haɗiye zancen a raina har sai bayan sallar isha'i da nasan Yaya Musaddiq ya dawo gida sannan na lallaɓa ɗakinsa na samesa, a wajen kamu kuwa Aunty Zakiyya ta samo kayan dana saka kawai........✍️ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒆𝒊𝒈𝒉𝒕_ ........Kai tsaye ɗakin Yaya Musaddiq na nufa. Bayan na gaishesa ya ɗan tsokaneni nai masa zancen da naji ana tsogumi ɗazun a kai. Murmushi yay min da faɗin, “Kandala ƙyale batun mutane da halinsu. Dan su basu iya komai ba daman sai gulma kawai. Yanzun nan babu jimawa muka rabu da Mansoor ɗin ma, dan munje can gidan nasa ne da kafintan da yay kayanki saboda zasu kaisu da sassafe gobe in sha ALLAHU. Ya kuma min batun kayan sai gobe in sha ALLAHU zasu kawo wata ƙanwar Mamynsu ce da zatazo da ga Dubai a yau da dare ake jira dan akwai wasu kaya a hannunta, amma shima yana cikin damuwar rashin kawo su shiyyasa ma ya kasa neman ko Hafizzullah a waya ya haɗaku dan kunyarki yake ji”.      Ajiyar zuciya na sauke a hankali. Dan nama san ƙanwar Mamyn tasu, yasha bani ita muyi waya. Murmushi yay min yana kai ma kaina rankwashi da faɗin, “Sam yanzu Kandala baki da kunya. Yanzu ni kike zuwa tambayar batun kayan aurenki ma”. Hannu na saka na rufe fuskata ina dariya. Shima dariyar yake yi. A dai-dai nan Hafizzullah ya shigo ɗakin da sallama. Dan tun washe garin da aka ganni yazo gida dama. Ledar hannunsa na warce ina faɗin, “Zaga gari mi kuma ka samo anan?”.       Ƙoƙarin warce ledar shima yake a hannuna yana hararata. Ban yarda masa ba har sai da na buɗe. Ganin awara yasa na taɓe baki ina miƙa masa. “Oh oh kwantar da hankalinka ashema naman talaka ce”.          “Oho dai, kema naga ci kike”.      “Ai ni in naci ba komai bane. Amma kamarka dai saurayi mai hurama ƴammata hanci abin kunya ne. ALLAH yau da ina da waya saina ɗauki hotonka nasa a status ƴan matanka sun gani”.      Dariya ya sanya da yimin gwalo, ya ce, “Ai sai ki samama kanki lafiya tunda baki da. Kuma sai na zuga Yaya Mansoor kar ya saya miki waya har sai kin shekara a gidansa”.         “ALLAH sarki jiki duk baƙin ciki su Hafizu. Aiko zakasha mamaki, kafin rana ita yau kasa a ranka na mallaki waya”. Na ƙare maganar ina kai masa rsankwashi a kansa. 💥💫💥💫💥💫      Kamar yanda Mansoor ya faɗa hakance ta kasance. Dan washe gari misalin sha biyu na rana ƴan kawo kayan nan suka iso gidanmu su uku. Zuwa lokacin baƙi sun ƙaru. Dan wasu matan ma a cikin ƴan Gwarzo ma sun iso. Tuni Aunty Zakiyya ta shiga maƙwafta tai kiransu dan Mum taki aikawa a kira kowa aiki. Sai ma yi take kamar wadda ta ruɗe. Dan ma ƙanwarta na tare da ita tana saitota. Baby kam ban san ina ta tafi ba dan tun jiya da yamma ban sake ganinta a gidan ba kuma. Waɗan nan kaya sun matuƙar girgiza sukata. Dan da gasken gaske Mansoor da ahalinsa sun nuna bajinta. Duk da ba fariyya akayi ba komai na nan dai-dai misali amma kuma na bajinta da zai tabbatar maka an kashe kuɗaɗe sosai. Dan komai acan-acan ko maƙiyi yasan kaya sunyi ga kuma kayan lefe da dama sun riga sun kawo.      Har aka gama karɓar kayan ni dai ban ko leƙo ba sam. Sai da dangin Mansoor suka wuce sannan aka maido kayan nan ɗakin da muke da su Gwaggo Gudidi sannan su Asiya suka tsareni sai na gani harda Aunty Zakiyya. Na ɗan kalla sama-sama na rufe akwatin ni dai. Har raina ina sake jin kima da girman Mansoor matuƙa dama ahalinsa gaba ɗaya....               💦💦💦💦💦💦💦       “Aunty dan ALLAH ki kwantar da hankalinki ni banga aibun yarinyar nanba sam wlhy. Ga danginta mutanen kirki. Karfa kiga irin tarbar da akai mana ta girmamawa wlhy.”          “Humm Anesa ni fa bance tanada aibu ba. Amma ya kamata ku fahimci abinda nake nuna muku. Yanzu dan ALLAH da kikaga yarinyar tayi kama da wadda akai kidnapping na tsawon sati biyu da wasu kwanaki? Nafa fiku son yarinyar nan, kuma har yanzu ina jin sonta a raina”.      “Aunty wlhy ni ban ganta ba.” “Humm to ai naso ki ganta da kin tabbatar. Amma al'amarin da mamaki ace ai kidnapping yarinya budurwa ƙyaƙykyawa kamar wannan wai ta tsallake tarkon namiji. Sannan kuma basu nema kuɗin fansa ba saboda sun sami abinda yafi kuɗin kenan. Ya kamata kowa ya gane maganar matar kawunta da abar a duba ce fa. Dan dolene ɗayan biyu a samu ɗaya. Kodai da ƙafarta tabi wanda suka sacetan nan zuwa wani hotel ko guest house. Ko kuma wanda sukai kidnapping ɗin nata sun samu abinda yafi kuɗi a jikinta. Wai Kinga kuwa yanda ta ƙara wani fresh na haske da laushin fata tamkar wadda ke rayuwa a ac. Ai bana jin ko kafin a sacetan jikinta yay wannan luf-luf ɗin. Amma da yake yaron nan ya makance da shirme shi ko sau ɗaya bai zauna yayi tunanin komai ba. Na rasa mike damun kan Mansoor ne. Ga ubansa shima yama ƙi ya sauraran balle ya gane abinda nake nufi. Kema kuma gashi kina nuna bazaki fahimceni ɗin ba”.          “A'a Aunty, ba fahimtarki ne bazanyiba nikam. Abinda kawai nake son ki duba bakin alƙalami fa ya riga ta bushe. Tunda gashi yau har sauran kayan lefe mun damƙa musu. Sannan Mansoor ya sanar min sun kai kayansu can gidansa wasuma a dangin nata na jerensu yanzu haka. Sannan Aunty gobe ne fa ɗaurin aure. Kuma kin ce Abban Attahir ma yaƙi fahimtarki balle ma shi Mansoor ɗin da kin gagara tunkararsa da batun, to tayaya kike tunanin zamu iya wani abu a ƙurarren lokacin nan?”.          “Zamu iya kuwa Aneesa. Dan anma zauna a filin ɗaurin aure ya watse ballema wannan da sai gobe. Mansoor da kike gani sam bashi da wani isashen wayo. Wlhy koda yasan yarinyar nan bata ƙwarai bace zai iya shanyewa saboda son da yake mata na masifa da ni sai a yanzu ma zuciyata kemin wasuwasin bana lafiya bane. Dan abun yayi yawa wlhy. Wace soyayyar haukace haka kamar wani labaran littafin hausa. Ku shaida ne nima naso yarinyar nan a baya, dan ina gaba-gaba wajen shawo kan Abban Attahir harya amince da auren nan duk da fama da aka sha sosai saboda dagewar da yay akan sai Attahir ya fara aure sannan Mansoor ɗin yayi. Amma magana ta gaskiya zancen matar kawunta na jiya ya dawo dani a hankalina. Sannan ganin yarinyar a cikin hayyacinta fes saima ƙyau data ƙara shima ya tsaya mun a rai. Dan haka shekaran jiya nace Mansoor ya kamata ya nema likita yasa a mata gwajin ciki amma yaron nan sai ya koma min wani kalar tausayi kamar zai yi kuka, yana faman roƙona nabar wannan maganar dan ALLAH kada wani yaji, shi yasan wacece Samraah. Da ace wata matsala ta faru da ita acan sai ta faɗa masa bazata munafuncesa ba. Kajimin yaro fa dan ALLAH”.          “Humm Aunty kar kiga laifinsa. Dan dama abin da kamar wuya ace ya fahimta kai tsaye. Amma dai kam al'amarin akwai ɗaure kai”.        “Bana wasa ba ma. Inda shi wani ne dan ALLAH basai ya haƙuraba, idan ma ya matsune yay auren dole a goben basai a ɗaura da Waleeda ba. Nasan dai Daddynta bazai ce komai ba wlhy”.       Idanu sosai ƙanwar tata ta waro waje. Sai kuma ta ɗan murmusa da faɗin, “Kai Aunty wannan ai babbar magana ce. Ni dai abinda nake gani anan kawai addu'a ce tafi dacewa. Sannan kisa a ranki in sha ALLAHU abinda zuciyarki ke ayyana miki bazai zama hakan ba.”       Baki kawai Mamy ta taɓe batare data sake cewa komai ba.....        💢💫💢💫💢💫💢💫💢    *_RANA BATA ƘARYA BILYN ABDULL. MASU IYA MAGANA SUN CE SAI DAI WAI UWAR ƊIYA TAJI KUNYA_*. Na yarda da batun masu hikimar zance. Domin kuwa nima da kaina na yarda wannan rana tawace kam. Sannan in har Mum na amsa sunan uwa a gareni to taji kunyar kuwa. Dan halayyar da take nunawa yasa dangin mahaifinmu suka gagara haƙuri sai da suka yayyaɓa mata magana. Dan har Kawu Lurwanu na iƙirarin mata dukan tsiya. Yaya Musaddiq ɗin da take gani aba komai ba a gareta ne yayta basu haƙuri da kareta har aka samu ƙurar ta lafa. Gida ya gama cika danƙam da mutane. Dangi na kusa dana nesa sun nuna halacci. Ga abinci kala-kala anyo daga Gwarzo batare da an zaman jiran sauraren na nan gidan Abba da kunya ta sakashi kawo buhun shinkafa a jiya da dare ba, sai wasu ƴan kayan miya cakwat da nama a baƙar leda abin zakkunya dai.         Kafin goma na fito shar dani a amaryata. Ga ƙunshin da ƙanwar mijin Aunty Zakiyya ta rangaɗa min a daren jiya ja da baƙi yay masifar fitowa kamar kaci. Duk da gyaran ƴan kwanaki akai mun na fito fes dani kamar fure a tsakkiyar lu'u-lu'u. Wani cotton lass ne a jikina lemon green ɗaya daga cikin kayan da suka kawo jiya aunty Zakiyya ta ciro min. Dan duk kayan da zanyi hidimar biki dama sai da Mansoor ya ɗaukan mukaje tela ya gwadani tun kusan wata biyu da ya shige. Aiko ɗinkin yay masifar zaunamin a jiki. Sai wata stones sarƙa mai ƙyalƙyali da walwali tamkar diamond na gaskiya. Awarwaraye zobba da komai sunji a hannayena. Ta sama gashina da a daren jiya shima yasha wanki daga ƙanwar mijin Aunty Zakiyyar dai dan aikinta kenan shima sai ƙyalli da ɗaukar idanu yake. Bayan ta gama tsaramin kwalliyar da naita zame-zame a farko aka naɗa min ɗauri na azo a gani. Nan take hasken camara na waya ya shiga kai-kawo a kaina. Nanfa wasu sukace sai sun turama ango fa. Ciki harda Hafizzullah. Ban tanka musu ba face murmushi kawai da nake yi........✍️          _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒐𝒓𝒕𝒚 𝒏𝒊𝒏𝒆_ ......Daga can tsakar gida kam taro yay taro gida ya kacame da hayaniya irin ta biki, anan ɗakin ƙawayena na zagaye dani. Wasu na hotuna wasu na kwalliya, wasu na hirarsu akan batun dinner da za'ayi bayan an kai amarya. Dan can gidan su Mansoor ɗinne suka shirya. Kiran da Yaya Musaddiq yazo yamin ne ya sakani saka gyale na rufe har fuskata. Shine ya kama hannuna har falon baƙi. Tunda muka fito kuwa gidan ya sake ruɗewa da buɗe-buɗe. Ni dai kaina na ƙasa a cikin gyale dan haka kawai sai naji ina jin kunya kowa.       Ban ida daburcewa ba sai da muka isa falon baƙi. Dan ganin kaf kawunaina na ɓangaren uwa da uba harda Abba. Sai gwagganni da innoni suma dai duk suna nan na kusa sosai. A tsakkiyarsu Yaya Musaddiq ya kaini ya zaunar ƙasan carpet. Shima sai ya nema waje ya zauna.        Kawu Musa ne ya fara min da nasiha mai ratsa jiki. Kafin sauran ma su dinga karɓa ɗaya bayan ɗaya. Daga baya suka koma faɗa da gargaɗi, yayinda ni kuma nike sharɓan kuka ta cikin gyale. Dan babu abinda ya tadamin hankali sai jin muryar Yaya Musaddiq na rawa alamar karaya sanda yake min addu'ar zaman lafiya a gidan aurena. Abba ma dai yamun tasa a taƙaice, daga baya kiran wayarsa da akai ya nema excuse ya fita, da alama kuma kiran da akai masan nada matuƙar muhimmanci ne. Dan naga sai da ya fara magana da Kawu Musa suka miƙe tare suka fita. Fitar tasu bai hana iyayena cigaba da mun nasiha ba, sai da suka gamsu sun min yanda suke buƙata kafin suka sallaman Inna Hauwa ta kamani ta maidani ciki, dan mazan zasu wuce massalaci ne daga can kuma za'a ɗauro aure. Dole sai da aka sake min kwalliya bayan nayi sallar azhar saboda na ɓata fuskar dan kukan da nasha. Kaya na canja zuwa wata shadda da taci uban aiki da stones sai walwali take yi. Ga ƙamshi irin na amare ƴan ƙwalisa ina zubawa. Acan ƙasan zuciyata kuwa jina nake duk wata iri kamar yanda aka san duk amarya da shiga irin wannan yanayin a irin ranar nan. Lokacin da ƙarfe biyu ke cika maza suka fara dawowa alamar an ɗauro auren gabana sai ya shiga wani irin luguden daka da sauri-sauri. Wani irin tsoro da fargaba na ratsa min cikin ɓargo da jijiya har ina jin wani kalar sanyi-sanyi duk da kuwa uban zafi ake zugawa a gari kasancewar watan azumin Ramadan na kawo jiki. Ƙawayena sun shiga min shaƙiyanci da buɗa a saman kai, sai na samu kaina da sakin hawaye masu zafin gaske da ban san dalilin yinsu ba. Shin murna da farin cikin mallakar matashin saurayi ƙyaƙyƙyawa ɗan ƙwalisa mai cikar kamala da dattako irin Mansoor ne, ko kuwa fargabar rabuwa da ƴan uwana biyu ne da ke a cikin tarkon wancan terror ɗin. Bily a lokacin sam na kasa ganewa. Na gagara banbance komai a yanda ya dace na fahimcesa. Sai ma wani sabon bugun zuciyar da na sake ji sakamakon shigowar aunty Zakiyya kamar a firgice tana kiran Gwaggo Gudidi data shigo tana miƙamin fura a kofi da aka dama wai na sha. Koda Gwaggo ta tambayeta lafiya, sai tace mata su Kawune ke kiranta kuma sunce tai sauri dan kamar dai akwai wata matsala. Da saurin kuwa ta fita alamar itama tana a cikin ruɗanin ne..        Na cigaba da zama kamar butun butumi a tsakkiyar ƙawayena daketa hotuna abinsu batare da su sun fahimci kamar akwai abinda ke faruwa ba. Muna nan dai shiru hayaniyar gidan na sake ƙaruwa alamar mutane na sake cika gidan ƙananun magana suka ɗan fara fitowa. Sai dai anƙi a fito da komai a fili ana ta son basar da mutane dai. Abinda ya ɗan fara tsayamun a rai shine rashin zuwan Mansoor gidan. Dan a burikanmu akwai zuwa hotuna bayan ɗaura aure da yace zasuyi shi da abokansa da kuma ni da ƙawayena da ƴan uwana. Amma dai zuciyata nata tausata akan masa uziri, dan maybe mutane sun masan yawan da hakan bazai yiwu ba ya cika wannan alƙawarin. Wannan tunanin yasa na danne zuciyata na ajiye wannan batun a gefe.       Isowar masu kiɗan ƙwarya bayan sallar la'asar yasa Inna Hussaina zuwa ta fita dani a ɗakin ni da ƙawayena. Sosai gidan ya cika da mutane har sai da naji ƙwalla ta cika min ido. Dan ban san munada taron dangi har kamar haka ba da zasu iya nuna wannan soyayyar garemu a irin wannan ranar. Ko a wajen kiɗan ƙwaryar ma duk da ba rawa nake ba tsaye kawai nake tsakiya ƙawaye na da ƴan uwana masu rawar zagaye da ni sai da dinga shigowa ana min liƙi, wasu kuma sukanyi hoto dani a waya harda masu video. Kusan ƙarfe biyar sai ga Gwaggo Magajiya riƙe da hannun Yaya Musaddiq da Hafizzullah wai sai sun min liƙi. Kallo ɗaya na musu su duka biyun na fahimci sunyi kuka. Dan idanun Yaya Musaddiq jajur suke. Na Hafizzullah kuwa har sun kumburo saboda shima fari ne kamar ni, dan mu biyun munfi Yaya Musaddiq haske. Hankalina ne ya tashi a take nima idanuna suka ciko da ƙwalla ina binsu da kallo. Amma sai suka ƙi yarda mu haɗa ido sai liƙi da sukemin kawai ana ihu kawunansu a ƙasa suna murmushin da ni kaɗai na fahimci na yaƙe ne. Duk yanda naso riƙe kukan nawa hakan ya gagara, bamma san sanda na riƙo hannayensu su duka ba cikin nawa. Dole suka kalleni a tare. Kukan na sakar musu kawai na faɗa jikin Yaya Musaddiq. Shima sai Hafizzullah ya ya rungumemu mu duka biyun ya saki nasa kukan. A take wajen yay tsitt, wasu na ganin mun birgesu da fassara abin namu da tsananin shaƙuwa ne da soyayyar juna. Wasu ko da suka san wani abu dake ɓoye sai suke jin tsananin tausayinmu da jin karaya suma. Nan take aka ringa tuno alkairan iyayenmu da musu addu'a. Dole dai Yaya Musaddiq ya jamu muka fita daga filin. Nan Gwaggo Gudidi ta jamu zuwa ɗakinsa ta dinga lallashinmu da mana nasiha. Haka kawai maganganun nata sai suke ta min kai da kawo dan na gagara fahimta da fassara wasu nikam. Kiran Yaya Musaddiq da akai a waya ne ya sashi miƙewa ya fita. Babu jimawa ya dawo yay kiran Hafizzullah. Anan ne Gwaggo ke tambayarsa lafiya? Sai yake sanar mata zasu maida kayan can gidan ne dan an gama kwashesu. Cikin nuna gamsuwa tace, “Oh to hakan yayi, bari na tattara su Zakiyya su sameku acan yanda aikin zaiyi sauri. In sha ALLAHU ai yanzu zakaga an kammala”.       Da to ya amsa mata yana ficewa. Hafizzullah ya canja riga suka fice. Babu abinda na gane a zancen nasu, amma na gagara haƙuri sai da nace, “Gwaggo kodai akwai abinda ke faruwa ne? Naga sai magana kuketa yi kamar a ƙudundune?”.          Kai tsaye tace min, “A'a babu komai ƴar nan. Kinga tashi mu koma ciki dan da anyi magriba zaki yi wanka a wanke wannan fentin da aka cika miki a fuska. Koda masu ɗaukar amarya dai sun zo ɗin sai dai mu yazam mune muka jirasu basu zasu jiramu ba”.     Banda tacewa face bin umarninta. Tunda dama nasan dai ya kamata a kainin da wuri kodan dinner da su Mansoor suka shirya. Amma kwalliya kona wanketa dole a sake wata basai munje can gidan ba kuma aita dibi-dibi nasan Mansoor da ƙosawa akan abu, sam baya son jira. Acan ƙasan zuciyata kam ina jin babu daɗi saboda rashin ganin duk jama'ar gidan a cikin sha'anin bikin nawa. Dan yaran duka babu wanda na gani har Auta da su Yaya Abbas da Nabel da shi banama zaton yazo gidan yana makaranta. Gara ma ita Mum ɗin bayan ɗaura aure sanda Yaya Musaddiq yazo ya fita dani ɗin nan zuwa falon baƙi na ganta ita da wasu ƙawayenta a tsaye sunata faman dariya da alama akwai abinda suke tattaunawa a tsakaninsu.        ★★Bayan nayi sallar magrib kamar yanda Gwaggo ta faɗa aka haɗamin ruwa mai zafi da kayan turaren ƙamshi a ciki nayi, koda na fito da taimakon Gwaggo na kimtsa jikina. Ta kuma tsareni sai da naci abinci da wani nama na musamman mai romo a cikin kula. Naman yayi daɗi dan haka na saki jiki naci sosai, koda tace sai na cinyesa ma ban musaba na dage na cinye nasha romon. Hakan yasa cin abincin bai armashi ba garan sosai. Tun ina kallon agogo harna daina. Sai dai a raina inata mamaki, dan tara dai-dai ya kamata ace muna a wajen dinner. Amma gashi anan har taran yama wuce ba'a kaini gidan su Mansoor ba balle ai batun zuwa dinner. Bily kar kiga kamar na cika zumuɗi ne fa. Kawai dai bana son naga an saɓama Mansoor alƙawari ne, to amma yaya zanyi, sai sanda aka kaini. Matsalata kawai da babu waya a hannuna.      Muna nan zaune Gwaggo na ƙaramin nasiha kusan goma saura akace su Yaya Musaddiq sun dawo sai a fito da amarya ga motoci sun zo. Sai a lokacin kuma naji duk na rikice. Nanfa na saki musu kuka. Duk yanda akaso na miƙe naƙi nai hakan har sai da Kawu Musa da kansa ya shigo yana faɗa sannan. Kuka nake sosai har numfashina na shiɗewa. Amma babu wanda ya saurareni, sai ma gaban Mum da aka kaini na roƙi yafiyarta. Cikin taɓe baki tana wani fisge-fisge ta ce, “ALLAH ya yafe mana baki ɗaya sai aje aita haƙuri, dama ita rayuwa ai haka take babu tabbas...” ganin tana neman sakin layi Gwaggo ta kamani muka fito. Abba ma an sake kaini na masa sallama. Yaya Musaddiq kam ya rufe kansa a ɗaki yaƙi yarda. Nasan kuka yake, dan haka nima na ƙara ƙarfin nawa kukan ina tutturjewa, amma babu wanda ya saurareni sai dai wasu nata bani haƙuri wasu na tayani matsalar ƙwallar aka fita dani. A rikicen da nake yasa bamma san kala ko adadin motocin da suka zo ɗaukata ba. Ni dai kawai an sakani a motar da ƙamshin da take yaso sakamin razani a zuciya, sai dai kuma rashin ƙarfinsa sosai da ruɗanin da nake a ciki na rabuwa da ƴan uwana ya hanani bama abin muhimmanci. Gwaggo Gudidi da Inna Magajiya ne tare da ni, sai gaba Ruƙayya ce ta office ɗin mu data zame min kamar babbar ƙawa ita da ƙanwar mijin Aunty Zakiyya........✍️ _🤭Uhummm inji mai ciwon haƙori._ _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_🐛TSUTSAR NAMA....!!🐛_* _(Itama nama ce)_ _𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_ _𝑷𝒂𝒈𝒆 𝒇𝒊𝒇𝒕𝒚_ .......Har muka iso kuka nake sosai, haka dai aka fita dani kaina a lulluɓe. Ina jin mutane nata yaba gidan. Hakan baisa naji wani abu daban ba saboda nasan gidan Mansoor kam tabbas yayi ƙyau da tsari. Sannan babu laifi babbane. Da addu'a na shiga kamar yadda Gwaggo ta bani umarni. Dan motar da aka ɗakkoni ce kawai dama ta shigo har cikin gidan. Sauran duk a waje suka tsaya. A falo aka ajiyeni kamar yanda Inna Magajiya tace. Mutane suka ɗan shishshiga kitchen da inda ba'a rasa ba. Bedrooms dai a rufe suke duka biyu dake a gidan kamar yanda naji suna faɗa. A karan farko na ɗan ji mamaki, dan nasan bedrooms huɗu ne a gidan Mansoor. Amma dai banda tacewa, bayan mutane sun gama zazzagawa suka fita dan dare ya farayi za'a maidasu gida. Sai da kowa ya fita sannan Gwaggo ta kama hannuna ta kaini bedroom da naji tana faɗa bayan ta buɗe da makulli, anan ne na gane ashe keys ɗin na hannunta sune dai suka hana mutane shiga wai dan kar a ɓata tunda dare yayi babu damar zama a gyara min. A bakin gado ta zaunar dani, tana sake jaddada min kalmar haƙuri, haƙuri dai da duk abinda zan gani, dan shi aure ibada ne bawai wasan yara ko nanaye kamar yanda mu yaran yanzu muke tunani ba. Ni dai kuka kawai nake zabga mata. Tadai samu ta zame jikinta ta gudu ta barni. Kuka na sake fashewa da shi irin mai cin rai da zuciya ɗin nan, harna zame na kwanta a gadon batare dana sani ba na cigaba da kukana.        Tun ina darzar kuka da tunanin Mansoor zai iya shigowa har al'amarin ya fara bani tsoro. Dan gari yay wani irin shiru sai kukan karnuna amma babu Mansoor babu labarinsa. Kai komai ya fara canja min daga yanda nake tunani da hasashensa. Dan daga jiya zuwa yau komai da nake gani ba irin tsare-tsaren Mansoor ɗina bane. Komai yana zuwa min a banbancin abinda muka tsara. Mi hakan ke nufi, Mansoor ne ya canja komai a yanda na sanshi ko yaya al'amarin yake ne?. Banda mai bani amsar ko ɗaya daga cikin tambayoyi na. Dan haka na cigaba da kwanciya a wajen ga ciwon kai mai tsanani na ratsani, kafin ma wani dogon lokaci na fara rawar sanyi. Ina jin yanda wata iskar hadari ke tasowa da ƙarfin tsiya amma na kasa ko motsi. Haka na cigaba da kasancewa a wajen na tsawon lokacin da ban san adadi ba har barci yay awon gaba dani batare dana farga ba....         Hasken rana irin mai kashe idon nan ne ya addabi fuskata. Dole na buɗe idanuna da sukai min wani masifar nauyi saboda kukan da nasha. Ganin a inda nake nada banbanci da inda na saba ya tuna min da mike faruwa. Zumbur na miƙe zaune ƙirjina na luguden daka. Ɗakin na shiga bi da kallo, madaidaici ne ba wani ƙato ba can. Sai dai kayan sun masa ƙyau cas. Abu na farko dana fara lura da shi sam ba irin fentin gidan Mansoor bane ba, kuma bedroom da Mansoor ya nunan a matsayin nawa randa mukazo ƙatone sosai. Ƙirjina yay wata irin girgiza. Sai dai tunawa da banyi sallar asuba ba yasa na tattare komai zuwa gefe na miƙe. Ƙofar da na gani da nakema zaton bayi ne na nufa. Nan ma dai ba irin toilet ɗin gidan Mansoor bane. Kai ƙwalwar kaina fa na neman juyewa. Amma dai na sake ƙoƙarin dakewa nayi alwala na fito. Akwatin dana gani saman bed side drawer na buɗe, na samu hijjab kamar yanda nai fata, dan haka na nutsu domin gabatar da salla..        Ina idar da sallar na miƙe kamar zararriya, dan kaina gaba ɗaya a juye yake da komai. Fitowa nai gaba ɗaya daga bedroom ɗin. Ganin wani dake a kusa da shi yasa na buɗe na shiga nan. Gabana ya faɗi. Dan babu komai a ciki sai ƙatuwar katifa irin wadda ba'a sanyawa a gadon nan. Sai wani ɗan ƙaramin akwati mai shegen ƙyau. sai takalma haif cover suma dai masu ƙyau sosai, a saman katifar da agogo da waya kusa da shi, sai can gefe kaya ne da aka cire shadda honey color data ciza sosai. Ga wani ƙamshi na musamman dake tashi har ina jin kamar nasan ƙamshin, amma dai na hana zuciyata hasasowa. Fitowa nai ƙwaƙwalwata na sake birkicewa. Falo ne dake tsaka tsaki, shima dai yayi ƙyau da kayan da aka jera masa, saukar idanuna akan wanda ke zaune daga can cikin ɗaya a kujerun dining ya saka zuciyata wata irin girgizar da ya rage kaɗan ta biyo ta bakina ta fito. Karkarwa jikina ya shiga yi, irin wadda bamma san na cigaba da tafiya ba cikin matuƙar sassarfa. Har na iso gaban dining ɗin bai ɗago ba. Yanata danne-dannesa a laptop hankali kwance. Ga mug dake ta turiri alamar shayi ko coffee a ciki.      “Wanene kai? Miya kawoka nan? Ina ka kaimin mijina?”.    Tambayoyi uku a jere suka fito a bakina dake rawa. Kamar baima jini ba, ko nace bai san da zuwana wajen ba. Dan ko motsi baiyi ba balle ya ɗago ya kallan, aikinsa kawai yake hankali kwance cike da ƙwarewa.           A matuƙar harzuƙe hawaye masu zafi na rige-rigen sakko mini cikin daka tsawa na ce, “Da kai nake magana malam!!”.    Cak ya tsaya daga danna keyboard ɗin laptop ɗin da yake yi. Nasan kuma yanda nai tsawar ne da matuƙar ƙarfi ga jikina na girgizar tashin hankali da ɓacin rai. Na sake zabura zan masa wata tsawar ganin nan ma bai amsa min ba yay wata irin juyowar da ta saka ni yin tsalle a lokaci guda da zuciyata saboda tsabar kiɗima. Sai gani rijif a ƙasa wanwar.        “Ba'a min tsawa”.     Ya faɗa a dakensa cikin silent voice ɗin nan nasa na gadara babu alamar damuwa da halin da yaga na shiga kuma. Sai ma ɗauke kansa da yay ya sake maidawa ga screen ɗin laptop ɗin. Yaraf kake jina na ƙarasa zubewa ƙasa gaba ɗaya. A hankali sai kaina ya fara juyawa, yayinda lips ɗina ke wata masifaffen rawa ina nunasa da yatsana da shima ke rawar. Tun ma ina banbance tsakanin haske da duhu har hakan ya fara neman gagarata. Tuni na tafi luuu ƙasa gaba ɗaya alamar ina neman suma. Daga haka ban sake sanin mike faruwa ba sai farkawa nai na sake gani na a inda na faɗin yashe. Da ƙyar na iya miƙewa hannuna dafe da kaina dake faman juya min. Kai tsaye inda nasan yana zaune na kai idona. Wayam babu kowa daga shi har laptop ɗin nasa. Sai mug ɗin nan na shayi kawai ajiye. Falon na juya ina sake ƙarema kallo. Yanzu kam ni kaɗaice a cikinsa da alama, sai zuciyata ke ayyana min kodai mafarki ma nake yi ne? A gaskiya sai dai mafarkin kuwa, dan wanda idona ya ganarmin a gidan nan nafi fatan ya kasance a mafarkin ne. Kasa daurewa nai, cikin layin juyewar kai tamkar wata ƴar maye na nufi ƙofar da nake ƙyautata zaton hanyar fita ce. Da ƙyar na iya lalubar handle ɗinta na buɗe, cikin yanayin dishi-dishi na dinga bin harabar gidan da kallo, ba wata babba bace dan bata wuce ɗaukar motoci uku ba suma a ɗan takure. Motar da nake ƙyautata zaton an ɗakkoni a ciki jiya kawai ce a ajiye. Saukar idanuna akan buzun dake zaune a gate yana fifita wuta alamar shayi yake dafawa yasa ni jin ƙarin gwiwar nufar can. Sai dai ina kai rabin harabar wani mahaukacin farin kare mai kama da tumakin turawa a gashi ko nace zaki a ƙarfi da girma ya wani irin zaburowa kaina daga inda yake kwance a saman motar yana haushi na hauka ga harshensa waje. Daburcewa nai na rikice dan na tsani kare. Balle irin wannan mara ƙyan gani da suffa, sauƙinsa ɗaya daya kasance fari. Ganin yana gab da iskoni na ƙwalla ƙara ina durƙushewa a wajen na ƙanƙame jikina dake rawar mazari.        “Laalah!”.      Aka faɗa a ɗan tsawace, sai dai hakan bai hana fitar muryar tasa acan ƙasan maƙoshi ba. Sannan karen ya tsaya cak bai ƙaraso inda nake ba. Sai kallonsa da yay yayi haushi sau biyu yana kallona kamar mai son masa ishara dani. Da alama ya fahimci mi karen ke nufi, dan a daƙile ya sake faɗi, “leave here”.      Abin mamaki tinƙas-tinƙas karen nan yabar inda nake ya koma saman motar daya taso yay kwanciyarsa kamar bashi ba. Sai lokacin na samu damar sake fashewa da kuma. Ganin ya juya abinsa zai koma inda ya fito na miƙe a zabure nima. Kusan atare muka shigo falon. Batare dama nasan mi nakeyi ba a tsawace na furta, “Ina ka kaimin mijina? Mi kayima Mansoor ɗina? Miya kawoka gidan aurena? Yanzun ma kidnapping ɗina kayi?”.          Bai ko kallan ba ya cigaba da tafiyarsa zuwa bedroom ɗin nan mai katifa. Ai bamma san lokacin dana daka wani uban tsalle ba nabi bayansa nima. Dan amsoshin tambayoyina kawai nake buƙata. Dole kuma ya bani, inba haka ba kuwa zaiga tsagwaron tashin hankali, kuma a wannan karon saina tabbatar masa da kaidin mace, dan ko dare bazan sake kaiwa a gidan nan ba. Ina isa ƙofar ɗakin yana rufota bamm, handle ɗin na kama da rawar jiki na fara murɗawa da jijjiga ƙofar amma ko motsi batai ba alamar ya kulle ta ciki. Wani irin kuka mai tsuma zuciya na sake fashewa da shi ina cigaba da jijjiga ƙofar da bugata a haukace amma mutumin nan ko tari baiyi ba. Galabaita ta sakani silalewa jikin ƙofar zuwa ƙasa wasu zafafan hawaye na rige-rigen sakkomin da masifar gudu. Cikin jin karaya da sarewa na shiga furta, “Awwab why? Why Maash? Why zakamun haka a ranar da tafi kowacce rana muhimmanci a garemu. Mike shirin faruwa? Ina mijina Mansoor?!! Miyyasa ka sake satoni zuwa nan a ranar auren...” kuka ya sarƙeni na kasa cigaba da maganar✍️   🤔🤔🤔😞 Alhamdullah 🙏. Anan zamu dakata a book one na wannan littafi mai suna TSUTSAR NAMA. sai kuma ALLAH yasa muna da rabon kaiwa bayan salla. ★Tofa masu karatu yaya take ne?. ★Mike shirin faruwa?. ★Ina Mansoor ango?. ★Miya kawo Maash a madadinsa? ★Kidnapping Sam-G ya sake yi kamar yanda take tunani itama kokuwa yaya al'amarin yake? ★Waye yay kidnapping Sam-G a farko tunda Maash ya tabbatar mana bashi bane?. ★Waye Maash ya kashe ma wai? ★Wake amfani da sunan Samraah wajen amsar kuɗi maƙudai haka a wajen Maash? Tunda tace ba ita bace. ★Maash zai samu nasarar amsar videon a wajen Sam-G kuwa? ★Magana fa ake ta an kawo amarya gidan mijinta amma ango ya rikiɗa zuwa wani daban. ★Hhhhh masu karatu akwaifa gurmi. Gurmi gagarumi ma kuwa na musamman. Dan littafin nan ɗauke yake da nasa salon shima. Hargitsi da cakwakiyar dake cikinsa kuwa. Hhhhumm ba'a magana, dan bama mu fara komai ba sai a book 2 da zai zo bayan salla, kuma komai da kuke buƙata yana a cikinsa ne. ★Dan shi kansa Maash fa akwai wani ƙunsashen al'amari a tashi duniyar dako fara taɓota bamuyi ba. ★Kai kar dai na cikaku da surutu, ku shirya kawai tsaff zuwa bayan salla idan ALLAH ya kaimu da rai da lafiya domin samun duka wannan amsoshin a TSUTSAR NAMA BOOK 2 har ma da wanda baku sani ba. ★Ya rabbi ka karɓi ibadunmu, ka gafarta mana ka yafe mana kurakuran mu. Ƴar uwa! Ɗan uwa! Duk wanda naima ba dai-daiba ya gafarceni. Nima na yafema kowa. Kada ka bari ko ki bari ku zama cikin jerin mutanen da zan iya kaima UBANGIJINA kuka a kansu a acikin wannan watan mai tunkaromu. Wannan shawara ce. Dan nima bazanyi fatan nazama cikin wanda kuma zaku kai ƙarata wajen UBANGIJINA ba. Fatana kumin addu'ar fatan alkairi nima na muku tare da iyayenmu baki ɗaya. Taku har kullum👎     BILKISU IBRAHIM MUSA             (Bilyn Abdull 💞) (C)2024. _Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._ _GUDA DAYA:400_ _BIYU:700_ _UKU:900_ _HUDU: 1200_ _BANK NAME:KEYSTONE_ _BANK ACC NO:6019473875_ _ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_ _ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_ __ _IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_ _*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_ *09033181070* *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* _MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*