Search
You have no alerts.

    507 Results in the "Hausa Novels" category


    • Kura a Rumbu – Chapter Forty-one Cover
      by Maryam Farouk (Ummu Maheer) A yayinda muke shirin kammala wannan littafi, idan kin san kina karantawa ba tareda kin siya ba kiyi ƙoƙari ki sauke nauyi domin babu lallai in yafe haƙƙina. Account details suna sama 🙏🏽🙏🏽 A hankali na buɗe ido na jin saukar abu mai sanyi a goshi na, ganin na buɗe idon ya saka Mama janye hannunta, ganin da tayi ina shirin sake komawa baccin ya saka ta ce "Da dai kin tashi haka nan kuma ki ƙarfafa jikinki tunda dai zazzaɓin ya sauka". Na yunƙura na zauna ina cije baki saboda kaina daya…
    • Kura a Rumbu – Chapter Fifty-seven Cover
      by Maryam Farouk (Ummu Maheer) BILAL Yana kwance a gida Hajja ta kirashi wai ya kawo musu kayan miyan da za'ayi tuwon ɗaurin auren Fadila da za'a ɗaura a gobe Juma'a. Da yake a tsini suke yayi mata laifi shiyasa bai musa ba ya tashi ya tafi kasuwar Yankaba ya yiwo musu cefanen ya tafi ya kai. Zagayewa yayi yaje ya samu Kawu Ɗayyabu, Yayan Hajja ne da suke uba ɗaya da yake mutum ne mara ɗaukar raini shiyasa duk rashin mutunchin Hajjan take shakkarsa ko da wasa kuma bata bari wani abu ya gilma a tsakaninsu shi Bilal ɗin yaje ya samu…
    • Kura a Rumbu – Chapter Fifty-eight Cover
      by Maryam Farouk (Ummu Maheer) HALIMA Cike da haushin Dr Salman na koma gida ranar Juma'ar, haka nan ya san banda mu zasuyi meeting ɗin amma ba'a gaya mana ba saida muka rigada muka je tukunna sannan babu damar tafiya haka mukayi zaman banza har sha biyu kafin muka tashi. Dama-dama da na ji na samu nayi clearance ɗina kafin na wuce gida. Bayan sallahr magriba Anty Labiba tace mu shirya muje gidan Uncle Mudassir yaronsa na biyu Khalil ya faɗi ɗazu da safe ya samu karaya, muna shirin fita Mama ta kirata tana tambayarta yaushe zamuje…
    • Kura a Rumbu – Chapter Fifty-nine Cover
      by Maryam Farouk (Ummu Maheer) Sai dana tabbatar ya fice daga building ɗin gaba ɗaya kafin na fita daga office ɗin ina kalle-kalle kamar mara gaskiya, ganin babu kowa ya saka na shige Elevator da sauri, a reception na haɗu da Juwairiyya ta kalleni fuska ba yabo ba fallasa kafin tace "Ina kika tafi tun ɗazu?" Wucewa nayi ba tareda na bata amsa ba ta sake cewa "Dr Sulaiman yana neman ki?" Na amsa da "Toh" ba tareda na tsaya ba na fita. A can kan hanya ya tarar dani, fuska ba annuri ya sauke glass yana kallona kafin ya ce "Get in".…
    • Kura a Rumbu – Chapter Sixty Cover
      by Maryam Farouk (Ummu Maheer) Ranar da Bilal ya kwana bakwai a Asibiti aka sallame shi sai Hajja wacce tun zuwan Fadila jikinta ya sake rikicewa sauƙin data fara samu komai yaja baya bata da aiki sai kuka da Allah ya isa ga Ahlan da tace ya yaudaresu ya auri autarta yaje yana azabtar mata da ita. Ganin jikin Bilal yayi sauƙi sai abinda ba za'a rasa ba ya saka aka sallameshi bayan likita ya ja masa kunne sosai akan kulawa da lafiyarsa. Sosai Zulaiha ke tsaye a kansa tana kulawa dashi, yanda Bilal yayi wani sanyi ƙalau lokaci ɗaya…
    • Son Rai – Chapter Eleven Cover
      by Aysha A Bagudo ... A hankali ya k'ai bak'insa daidai saitin Kunnenta ya soma rad'a mata magana Cikin Sanyayyiyar muryan shi mai tsananin kashe mata jiki, da tsuma zuciyarta . "Yesmin...... bazan i'ya abinda kike tunani ba a halin yanzu da zuciyata take cikin garari da tashi hankali ,bama haka ba har a cikin zuciyata bana so wani abu ya sake Shiga tsakanina dake..... nayi nadama har a cikin Zuciyata, Nayi nadama! nayi nadama!!! " bana son wata halaka ta sake shiga tsakani na dake matukar baki kasance mallakina ba…
    • Son Rai – Chapter Sixteen Cover
      by Aysha A Bagudo "Yayinda a hankali suka sakarwa junansu murmushi mai tsuma zuciya da aikawa ruhi wani sako na daba . " lokaci day'a kuma murmushin yesmin ya koma kuka cikin sanyin murya mai cike da kuka ta soma magana "why D ? "Me yasa ka min haka ? " Me yasa kayi nisa da rayuwata alhalin kasan zuciyata bazata iya d'aukar rad'adin hakan ba ? " lumshe idanunshi yayi saboda wani irin yanayi daya tsinci kanshi na zallar shaukinta , muryarsa a kasalance yace "Kiyi hakuri yesmin di nah , Ni kaina ban so tafiyar nan ba,…
    • Son Rai – Chapter Eighteen Cover
      by Aysha A Bagudo Bayan sun gaisa da abban yesmin , Dr Jamil ya d'an saurara ,yaji ko yesmin zata gaishe shi kamar Koda yaushe . amman yaji tayi shiru taki cewa komai ,hakan ne yasa shi maido hankalinsa da idanunshi har ma da natsuwarsa inda take zaune kusa da mahaifinta ,ya tsura mata idanunshi masu matukar kyau da tasiri a jikinta har ma da zuciyarta .... "Zuciyar ce ta dinga dokawa da mugun karfi , sakamakon idanunshi da take jin yana yawo a sansar jikinta, cikin wani irin yanayi na bugawar zuciya ta d'ago kanta ta…
    • Son Rai – Chapter Six Cover
      by Aysha A Bagudo *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE* . ....Ita kuwa yesmin ta'ba kofar bathroom din , da akayi, yayi mugu mugun hargitsa mata 'kwal'kwaluwa ,har ta saki k'ara mara sauti batare da tasan tayi hakan ba, jikinta na sake d'aukar kyarma, dan daman tana manne da jikin kofar ne ,ta manne kunnenta tana sauraran tautaunawarsu , daki daki komai ke shiga kunnenta tun daga kan maganar jakarta da mahaifinta yayi har zuwa Sauran maganganun ... A matukar…
    • Son Rai – Chapter Nine Cover
      by Aysha A Bagudo *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE* . ...ganin yanayin halin da yesmin take ciki , yasa hankalin Dr Jamil yayi mugu mugun tashi. ,aiko take jikinsa ya kama rawa, gumi ya shiga tsatsafo masa ta ko ina a sansar jikinsa, muryarsa can kasa tamakar ta marayan zaki ya Kira sunanta "yesmin !yesmin !! Yesmin !!! "Dan girman Allah ki tashi karki min haka ,girgizata ya shiga yi, Yana Kiran sunanta ahankali amman shiru yesmin taki motsawa , sai jikinta…
    • Son Rai – Chapter Twenty-five Cover
      by Aysha A Bagudo "Zuba masa ido kawai Dr jamil yayi yana cigaba da kallonsa zuciyarsa na harbawa , Shima abban yesmin din kallonsa yake, yana jin abubuwa guda biyu a lokaci day'a a kanshi farinciki da bakinciki . bangaren Dr jamil Shima zuciyarsa cike take fal da tashin hankali bai ta'ba tunanin faruwar abinda ya faru a safiyar yau din ba ,yau tazo masa da abubuwa da yawa ,tashin hankali da farinciki mara misaltuwa " sai dai har lokacin zuciyarsa rawa take ,ya kasa tabbatar da abinda aminin nasa yayi masa…
    • Son Rai – Chapter Ten Cover
      by Aysha A Bagudo ..A k'alla Umma ta kusan minti goma tsaye a bayan kofar , kafin daga baya cikin firgici ta maida idanunta da hankalinta a kan Yesmin dake daf da kaiwa k'asa towel d'in dake d'aure a jikinta na k'ok'arin zamewa kasa . A matukar tsawace Umma tace "ke Yesmin ....wata irin zabura tayi ta saki razananniyar k'ara ta k'arasa zubewa k'asa kirjinta na dukan uku uku , jikinta na kyarma runtse idanunta tayi gam saboda tasan mai afkuwa ya rigada ya afku.... tasan Ummanta ta rigada ta gama ganin komai.... "yau…
    Note
    error: Content is protected !!