Search
You have no alerts.

    Samarin Bana Chapter 3

    03

    [11:10PM, 10/11/2016] Rahamat Nalele 👯:

    Dake SAILUBAH Tace kanta na mata ciwo sai kawai KHAMIS yasha Sha taletale ya fara saukesu ita da RAMADAN

    Sannan yakai XEE ya wucce gida 

    Aranar ne aka ‘daura Auran Saudat da mijinta Aminu

    Qarfe bakwai RAMADAN yana gaban SAILUBAH yana lallashinta tatashi aje kai Amaryar da ita

    Tace dan Allah karabu dani kaina namin ciwo

    Yace haba Auntyna bata da qawar da tawucceki pls dan Allah badan niba tashi kije

    Sanin halinsa da naci yasata tashi tayi wanka tashirya kicin wasu riga da siket na atamfa sun amsheta matuqa

    XEE tayi dariya Tace aigwara da ‘dancin naki yasaki tashi dan abinda kikasoyi Sam bai dace ba

    Ta feshe jikinta da turare suka fitoh

    Lokacin yayi daidai da xuwan angwaye masu ‘daukar amarya

    Nan samari masu ji da kai suka yimusu cah akai wannan Yace sushiga motarshi wannan Yace tashi

    Ahaka dai suka shiga motar wani Abbas yajasu Cikin sauri sanda ya fitta daga layin ya fara tafiya ahankali

    Ya kalli XEE Yace qawarki tayimin dan Allah kiban ita

    Tayi murmushi Tace indai SAILUBAH ce nabaka ita

    Nan yacika da murna yace xan iya samun numbarta Tace eh mexai haka

    Ahaka yadinga Jan XEE da xance tana biye mishi duk akan SAILUBAH ne

    Tana jinsu tayi shuru

    In ta ‘kaice muku awannan daran SAILUBAH tayi samari kusan shidda masu aji da nera

    Kuma sanda suka Nace suka samu numbarta

    Dukda ba magana take musu bah. XEE CE take aran bakinta

    Gidan Amaryar Saudat yayi kyau Sosai dan Babban gidane. Saidai tana da abokiyar xama Rabi’a…..

    Abin takaici😔

    Sunfito xasu koma gida. motar Abbas suka shiga inda yajasu sun hau titi yana jansu ahankali dan bayaso yadena kallan masoyiyar tasa SAILUBAH

    Basai XEE tahango saurayinta Surajo da wata mace a motarsa ba. Kasan cewar sun kunna wutar motar yarinyar tana duba wani book dake hannunta

    Kallo ‘daya xaka musu Kasan suna cikin nisha’di.

    Gaban XEE ya fa’di  hankalinta ya tashi toh dama XEE kishine da ita Sosai akan sahibin nata Surajo

    Aiko cikin qara Tace Abbas yabi mata Su

    Cikin rashin fahimtarta ko ya bishi

    Har suka kai wata unguwa wai ita bacirawa inda sukayi parking a’kofar wani gida

    Abbas ma yayi parking kusa dasu

    Cikin Xafin nama tayi yunquri fitta daga motar…  SAILUBAH tariqe hannunta Tace karkiyi wani abu pls kibarsu mukuma gida

     cikin xubar da hawaye Tace naga alamar bakisan kishi bah bakisan miye so ba. Tunda baki ta6a tsaida mutum ‘daya ya mantar dake duniyar marasa SOO bah

    Wlhi kinji na rantse miki ‘daukewar numfashine kawai xai hanani xuwa ga waccan maci amanar

    Nan tafuzge hannunta tafuta daga motar

    Tana xuwa ta kwankwasa musu gilashin motar

    Budurwar tabu’de tana fa’din kai karima kincika naci toh munsiyo miki ice-cream ‘din

    XEE Tace karimar uwarki……..

    Aiko da sauri Surajo ya fitoh daga motar cikin tashin hankali danjin XEE Yace meya kawoki nan My XEE

    Cikin maseefa Tace sunan nan ya fitta daga bakinka

    Munafiki axxalimi makiri dan iska ni xaka yaudara

    Kana tare dani. Kuma kowane lokaci fa’damin kake ni ka’daice budurwarka.

    Ashe qarya kake.

    Ta fashe da kuka tana fa’din na tsaneka

    Kasa nabaka yardata gabaki ‘daya….

    Yau Aurena da kai saura wata biyu amma kake Neman wata……

    Kuttumar uba  Auran ki dashi wata biyu

    Budurwar tatambayi XEE da mamaki

    XEE tamata mugun kallo Tace bagaki gashi ba Ki tambaya shi man

    Cukume wiyan rigarsa budurwar tayi cikin tashin hankali Tace idan kasaba yaudarar mata ni baka isa ka yaudareni ba

    Saura sati biyu Aurena dakai ashe kanacan kana neman wata harda kai sadakinta ‘dan rainin hankali ni xaka rainama wayo…..

    XEE ta qara tsaida idanta akansa cikin sanyi Tace abinda Tafa’da gaskiya ne

    Yayi shuru duk ya burkice

    Tayi murmushin takaici Tace kaxo gidanmu ka kar6i sadakin ka na tsaneka…..

    Tana fa’din hakan tayi cikin motar Abbas yajasu suka bar gun

    Duk lallashin duniyar nan ba wannan SAILUBAH batama XEE akan tayi shuru tayi kuma hakuri ba Amma taqi sauraranta

    Haka Abbas ya kaita gidansu Sannan ya juyo da kan motarsa ya dawo da SAILUBAH gida

    Akan idan RAMADAN yayi parking 

    Yace toh Allah ya tashemu lafiya dan nasan baxa ki tsaya saurara taba awannan lokacin sai munyi waya

    SAILUBAH tamai murmushin yaqe Tace toh. Dan ba qaramin ciwo kanta yake mata ba

    Tana shiga gidan nasu RAMADAN ya bita har ‘dakinta

    Yace shi kuma wannan Waye

    Ta kallesa ka’dan Tace ban sani bah

    Yanayin da tayi magana dashi shiya tabbatar mishi ciwan kan nata bai saketa bah

    Dan haka ya bu’de dirowar da take saka magun gunanta ya ‘dauko mata maganin ciwan kan ya bata da ruwa. Sai taqi kar6a

    Sam SAILUBAH batasan magani danjinsu allura

    Dake yasan da xaman wannan sai yahau lallashinta akan tasha

    Tace nace baxan shabako. ko Ana dolene

    cikin fusata Yace Wlhi saikin Sha so kike Ki hanani bacci cikin nutsuwata

    Ta kalleshi cikin qarfin hali Tace wai me yasa kagama raina nine RAMADAN

    Yace ba rainaki nayiba Auntyna kawai dai Kinsan baxan iya bacci bane kina Cikin ciwan nan dan Allah dan Annabi kisha kitemaken

    Sarai tasan inba Sha tayiba baxai barta ba. Kuma da gaske baxai iya yin baccin ba

    Dan haka ta kar6a tasha kamar xatayi kuka

    Yayi Murmushi dan yasan ba qaramin sa’arta yaciba wajan shan maganin da tayi

    Sanda ya barta nakusan minti goma Sannan Yace dan Allah Auntyna Waye Wanda ya saukeki amota

    Ta xubamai ido Tace miye damuwarka RAMADAN dan Allah

    Baxaka tausayamin cikin wannan halin da nake cikiba saika dameni da surutu

    Ya sosa qeya Yace Wlhi nafi kowa damuwa da duk ciwan daxai cafkeki

    Amma dan Allah kitemaken kigayamin Waye shi

    Tace me sona ne

    Yace tab yanxu kina sanshi kuma

    Ta kallesa Sosai Tace ai kallo ‘daya na mishi naji ina sansa har cikin xuciyata

    RAMADAN ya galla mata wata muguwar harara batare daya San yayiba Yace hmm

    Lalle bakiyi sa’ar masoyi ba

    Tace meyasa

    Yace kallo ‘daya na mishi nasan bai cika sharu’dan da kikeso agun Wanda kikesan aure ba

    Tashi tayi daga gadan nata Tace me ka hango  atare dashi wanda bai cika shara’di na ba. Bayan yana da ku’di daga ganin motar daya ke tuqawa. kai ka sani

    Yace eh da alama me ku’dinne Amma Wlhi xakisha kunya duk ranar da kika fitoh dashi kika nuna ma jama’a shine mijin da xaki Aure

    Ta waro ido. Me kake nufi

    Yace yayi muni da yawa ga Wasu haqora da suka mishi cakaro cakaro abakinsa

    SAILUBAH tayi shuru tana so ta hango Abbas a idanta Amma takasa dan ita ba kallan tsaf tamasa ba

    Kuma dama tacema RAMADAN tana san shine dan ya barta da surutunsa kanta namata ciwo

    Ganin da RAMADAN yayi tashiga tunani shiya sashi shafa gefan fuskarta tuni ta farfa’do daga tunanin nata

    Yace gaki kyakkyawa abinki Amma xaki Auri me kama da aladu….😆

    SAILUBAH ta shagwa6e fuska Tace kai ni har naji na tsane shi

    Yayi Murmushi Yace innine ke Wlhi in yaxo gobe baxan futa ba……

    Taqara shagwa6a fuska Cikin shagwa6a Tace yanxu kenan idan yaxo gobe karna fitta

    Yace in nine ke ba

    Tace nifah bana san Auran mummuna

    Yace na sani ai. mexai hana kice mishi ammiki Miji

    Ta qura mishi ido tana san tunanin wani abu. yayi saurin katse mata tunanin da cewa no fah. ki fita idan yaxo Amma kiqare mishi kallo Wlhi xaki yarda da xancena. Yafa’da yana mai miqewa har yakai ‘kofa. Tace ina fatan dai kaci abinci. Yace banci bah dan abincin biki ne agidan

    Tace ai yayi da’di

    Yace tuwan 😳

    Da suka sama miyar kabewa kai Gaskiya ba xanci ba Wlhi. Dan natsani kabewar nan

    SAILUBAH tayi Murmushi dan tuno qiyayyar dake tsakaninsa da tuwo. Sam ya tsani tuwo musamman asaka kabewa amiyar (kunsan kano da kabewa Allah ya basu hikimar sarrafata😆 )

    Tace ka tsaya in dafama ko indomie CE

    Ya dawo ya kama hannunta Yace baki da lafiya Auntyna ki barshi. xansa momy ta dafamin. Ina san kihuta banasan Ki wahala kinji

    Tace toh ‘daukar min alqawarin xakaci

    Yayi Murmushi da jefanta da wannan shu’umin kallan nasa

     Tuni gabanta ya fa’di tanemi rikicewa

    Ganin haka yasashi shafar gefan fuskarta Yace na’dau miki alqawari xanci.

    Shuru tayi harya bu’de ‘kofar xai fitta cikin wata wahalalliyar murya Tace dan Allah kar kaje club yau

    Ya san idan ya qara gigin kallanta tabbas xai hanata bacci yau

    Dan haka batare da ya juyo ba Yace toh naji

    Alkawari

    Nayi

    Ya fitta daga ‘dakin

    SAILUBAH sai taji hankalinta ya kwanta dan tasan tunda Yace baxaije bah toh baxai je ‘dinba

    Kwantawa tayi tafa’da tubanin XEE

    Allah Sarki yanxu haka tanacan dana kukan nata

    Tayi Murmushi wai miyema soyayya ne

    Sam SAILUBAH batasan soyayya ba

    Dan tana fara soyayyar RAMADAN yake katse mata jin da’dinta

    Ita dai abinda yake gabanta shine Auran me ku’di

    Ahaka bacci 6arawo yayi awan gaba da ita

    RAMADAN ko yana kallan Su FAWAS na shirin xuwa club Yace baxai jeba

    Sukace me yasa Yace Auntyna ta hanani xuwa yau

    Kai Aunty LUUVAH me yasa tayi haka. Cewar KHAMIS

    FAWAS Yace share kawai muma mun fasa xuwa.

    RAMADAN yayi dariya Yace nasan xa’ayi haka

    KHAMIS yajah tsaki Yace naso hutawa Wlhi

    Dole haka sai gun ‘yan matan nasu sukaje kawai 

    XEE ko tasa iyayanta tayi agaba tana musu kuka

    Da tashin hankali suke tambayart lafiya

    Nan tagaya musu Komai taqara da cewa Wlhi BABAH na tsani Surajo. Bana sansa. Kurku ha’da ni Aure dashi dan baxan ta6ayi masa biyayya bah

    Kuma ai ana Aure ne dan biyayya Wlhi mamah baba baxan ta6a yimasa biyayya ba nidai bana san shi yanxu

    Dake iyayan nan ne masu San ‘ya’ya nan suka hau lallashinta da cewa gobe xasu aika masa da sadakinsa basai ma yaxo bah

    Nan hankalin XEE ya kwanta

    Takira SAILUBAH take gaya mata yanda tayi da iyayan nata

    SAILUBAH Tace Wlhi banso rabuwarku bah dakun sa santa kanku dai da yafi

    XEE tajah tsaki Tace Wlhi Sam SAILUBAH bakiyi bah

    Da Kinsan xafi da ra’da’din da nakeji araina da baki CE haka ba

    Washe gari misalin qarfe biyu ne suke da lectures

    Dan haka RAMADAN ya biyoma Auntyn nasa

    Ta kallesa da kyau Tace baxan iya xuwa bah

    Yace Amma gaki garau mexai hanaki xuwa 

    Tace ni nasan abinda nake ji

    Yace Auntyna akwai ranar da xaki nemi karatun nan ido rufe Ki rasa shi

    Me yasa bakya san karatu ne Auntyna. yana da amfani fa. Wannan CE damarki idan kika bari takubce miki ya wucceki kenan har abada

    Duk da in san karatu irin na Aunty XEE tafiki

    Amma da antashi magana sai kice wai aibake ka’dai bace kike qin karatun

    Ta galla mai harara. Cikin raini tace wai in tambayeka man

    RAMADAN ya faketa da ido. Taci gaba da fa’din

    Ni da kai waye babba

    Yace ke

    Tace meyasa kake sani agaba da fa’da sai kace Kaine Babban nice qanwar

    Yace Auntyna kin kasa ganewa Sam.

    Shi karatu idan yaxo gareka kamashi kake da kyau dan kai kake da cin moriyarsa. Ina guje miki ranar da xakiyi Aure kisami Miji me in barin Matarsa fita karatu. Ya hanaki cigaba alokacin dake kike ganin dacewar hakan

    Tace na rigada nagama tsarama kaina rayuwar aurena. Insha Allah xata xomin yanda ya dace

    Yace koh

    Tace kwarai

    Yace amma inaji ajikina baxaki samu yanda kikeso ba

    Ta galla mai wata muguwar harara tace insha Allah xan samu fiye da yanda nake so mugu kawai

    Kaga kaje kawai karka tsaya cikani da surutu ‘dan rainin hankali kawai. Ta qarashe da nuna 6acin ranta

    Yayi Murmushi Yace toh shikenan Allah yabaki lpy Auntyna saina dawo 

    Har yakai kofah Tace RAMADAN Yace na’am.

    Taqara harararsa Tace kayi kyau Sosai. Tafa’da batare da tasaki fuskarta ba.

    Yadawo gareta ya kama hannunta da shafa goshinta. Ba xafi agoshin Yace Allah yabaki lafiya Auntyna kema kinkyau Sosai

    Tace kaci abinci ko Ya’daga mata kai alamar eh kana ya mata kiss a hannu ya fitta yana cewa natafi

    Tabishi da kallo tana jin da’din qamshinsa.

    RAMADAN yana futa bai da’de ba Abbas ya yaxo gidan

    Da sauri  SAILUBAH takeyin shiri burinta taje taga munin Abbas ‘din da RAMADAN yace

    Aiko bayan sun gaisa  ta qura masa ido……..

    Eh Gaskiya ne

    shi baqine bai cika kyau ba. Kuma da gaske yana da hakwara Amma basu sashi muni bah. Yanda tadinga tunanin xata gansa abin bai kai haka ba. Dan yana kyansa daidai gwargwado

    Amma taji aranta Sam bata sanshi dan maganar  gaskiya RAMADAN yayi nasarai jefa mata qiyayyarsa

    Yace ya kikayi shuru haka kina kallona

    Tace hmm ina takaicin abinda xan gaya maka ne

    Yace duk abinda xai futo daga bakinki baxai ta6a xama takaici agareni bah

    Tace ina da mijin Aure na…….

    Da sauri ya kalleta cikin wani hali Yace maganar gaskiya kike gayamin dan…….

    Ta katse shi da fa’din. Baxan maka qarya ba

    Yayi shuru cikin wani yanayi narashin jin da’di

    Can Yace toh Allah ya ha’dani dame kamarki ina barin nan

    Tace ina maka fatan samun wacce tafini

    Yace Nagode

    Haka tana kallo ya juya motarsa yabar harabar gidan nasu

    Tana shiga ‘dakin Kakah  kiran XEE ya shigo wayarta

    Tace ya akayine XEE

    Daga can XEE Tace hmm Ki saurari xuwana Tace Allah ya kawoki ta ajiye wayan

    Kakah Tace yadai jikin naki Tace da sauqi. Tace Toh Madallah

    Dama inasan cin tuwan dawa ne miyar ku6ewa. SAILUBAH tafa’di hakan cikin marairai cewa

    Kakah Tace toh ai sai ayishi yau

    Kusan qarfe shidda da rabi 6:30pm XEE taxo gidan nasu

    Tace qawata ina cikin wani hali

    SAILUBAH Tace ai in baki shiga ba a tambayeki dan rabuwarki da Surajo lokaci ‘daya ba abubane wanda xai barki haka cikin Sauqi

    Tace Kin san Allah na manta da wani Surajo dan nariga da nacireshi kwata kwata daga raina

    Ni damuwata itace KHAMIS

    Wayyo Allah na  SAILUBAH yau yarannan ya rikitani

    Ya jefamin sanshi araina lokaci ‘daya

    ashe dama duk wannan burgenin da Nake cewa yana yimin Ashe na fara sanshi ne dama haka so yake shiga xuciyar mutum farat ‘daya

    Wayyo ni XEE yaxanyi dasan Wanda na girma qaramin yaro

    Saiga hawaye ya xubo mata

    Cikin kuka tacigaba da fa’din watoh nafito daga department ‘dinmu ‘daxo ina tafiya ahankali dan wata gajiyace ta kamani lokaci ‘daya

    Ban kalli gabana Sosai ba. basai kawai nayi tuntu6e ba. Nayi taga taga xan fa’di.

    Sai gashi ya yanko kwana……

    Cikin sauri ya kama hannuna da janyoni  jikinsa.

    SAILUBAH Kaina ya sauka a qijinsa

    SAILUBAH na shaqi qamshinsa

    SAILUBAH saida xuciyata tabuga hankalina ya tashi dan jin wani fitinannan filing daya kusantoni

    Sunkwi da kanta XEE tayi

    Tayi shuru agun hawaye yana cigaba da xuba mata

    Kana ta’dago ta kalli SAILUBAH da tasaki baki ido hanci tana kallanta

    Tace wlhi jinayi dama in dauwama a haka a qirjinsa dan jin yanda qamshinsa yake shiga hancina

    Daga nan saime….. SAILUBAH Tafa’da cikin buqata hankali tashe

    XEE tajah numfashi Tace daga nan sai yayi saurin sakeni cikin ‘dan nuna tsoro Yace am sorry Aunty XEE nayi abinda bai dace bah dan Allah kayi hakuri

    Nayi shuru ina kallansa

    Ya marairaice tamkar xaiyi kuka kamar yanda RAMADAN yake miki inya miki lefi. yaci gaba da fa’din. Xan shiga damuwa idan bakiyi magana bah

    Nace hmm karka damu Bakomai bakayi abinda bai dace ba. Daka barni ai dana sha qasa Qanina

    Yace Yauwa dama naxo induba ko kin fitone. Mutafi in saukeki agida sai kuma naga RAMADAN Yace min kina fitowa yanama Cikin motar ma

    Nace toh muje

    Kinsan Koda muka shiga motar sai Satar kallansa nake. Yayinda shi kuma ya sake sunata hira da RAMADAN

    Ahaka suka saukeni suka kaqara gabah

    Ayanxu dai haka Wlhi SAILUBAH damuwata ‘daya shine inga KHAMIS ko hankalina xai kwanta

    SAILUBAH ta galla mata harara Tace wai ina hankalinki ya tafine.

    Ya xaki SO qaramin yaro dan xubar da aji

    Yanxu ke kanki bakiji wani iri da kunyar  gayamin da kikayi ba

    Kalleki mace har mace Amma kirasa wanda xai burkita miki kwanya sai KHAMIS qaramin yaro

    Kina wani maganar ya rungumeki ni runguma nawa RAMADAN yayi min akan hakan

    Kin san ta6a hannuna agun RAMADAN  bakomai bane

    Ya riga da ya sabarmin da hakan

    Idan kuka nake rungumata yake yana lallashi inyi shuru. Haka idan shi yana cikin damuwa kwantar da kansa yake ya shagwa6e tamkar jariri in lallashi

    Agabanki yasha yimin kiss a kumatu a hannu Amma ni meyasa banji san shi ba

    Eh idan ya ta6ani inajin xirrrr Amma ban ‘dauki hakan a matsayin Komai ba dan dama bansa wani abu araina bah

    Kawai kinbi shshashar xuciyarki kinfa’da soyayyar qaramin yaro waima KHAMIS.

    Tsaki XEE taja cikin takaicinta Tace hmm to dama ke me xakiji Bayan ba sanin soyayyar ki kayi ba

    Sam bakisan miye soyayya bah

    Kina maganar na kamu da soyayyar qaramin yaro ai bani na halicci xuciyata bah

    Inasan KHAMIS kuma Wlhi in ban Auresa ba baxan ta6a yin Aure ba kinji na rantse

    Cikin Baqin ciki hawaye ya xuboma SAILUBAH Tace ai sai kije ki nemama kanki mafuta. Tafa’da da Takaici

    XEE takalleta Tace ki fahimce mana. Wlhi SO matsifane so balaqi ne. Shuru SAILUBAH tayi mata

    Haka XEE taqarashi kukunta ta hakura tatafi dan SAILUBAH Sosai takasa fahimtarta.

    Koda RAMADAN yaxo gun SAILUBAH bai sameta da warwala ba sai yayi tunanin ko dan rikicinsu na ‘daxo ne. Yace waya ta6amin Auntyna. Taqi kulashi

    Cikin kalar tausayi Yace Wlhi in bakiyimin magana bah Xanyi kuka

    Ta kallesa. Dariya ta kamata. Toh kayi mana.

    Yayi Murmushi ai kuma ya wucce tunda kinyi maganar harda dariya pls meyake damunki. Ko wancan mutumin yaxo ne kuma kinji kina sansa haka a munin nasa

    Ta 6ata fuska cikin shagwa6a Tace hmm yaxo Amma Nace mishi inada mijin Aurena

    Cikin farin ciki Yace Allah Auntyna

    Tace Wlhi

    Yabata kiss a hannu Yace Yauwa gwara da kikace mai haka

    Da xakiban dama da kin samu Wanda ya dace da ra’ayinki.

    Tace kamar ya

    Yaje feta da kallan nan nasa. Nanko jikinta ya mutu ta rikice mai

    Dama haka yakeso danya samu yanda yake so

    Hannunsa cikin nata idan shi ma cikin nata Yace so nake duk wani saurayin da kikayi Ki fa’damin dan in tayaki gano Wanda ya dace dake da kuma ra’ayinki

    Ya rigada ya gama kashe mata jiki saita ‘daga mai kai kawai alamar toh

    Yayi Murmushi da ficcewa daga ‘dakin dan yasan hirar tasu taqare tunda jikinta ya mutu

    Shuru SAILUBAH tayi ta bishi da kallo harya fittan

    Kana ta kwanta tana tunaninsa

    👯👯👯

    Sun ha’du Su uku kamar yanda suka saba dan xuwa club. Amma sai FAWAS Yace suje gidansu  Aymana budurwarsa

    Nan sukaje

    tafitoh cikin nutsuwa. Yarinya ‘danya shakaf.

    Join our WhatsApp Group Here

    0 Comments

    Heads up! Your comment will be invisible to other guests and subscribers (except for replies), including you after a grace period.
    Note
    error: Content is protected !!