Search
You have no alerts.

    Riqqon Kaka Chapter 4

    RIKON KAKA

    CHAPTER 4

    Kaka tai sallama qofar shagon Malam salisu mai

    tireda, dattijon mutum mai mutunci ya fito daga

    shagon yana fadar.

    “A’a Hajiya, sannu da zuwa, yau kece da, kanki?

    Ina jikar taki?”

    Kaka tace, “‘Yarka tai mata dukan kawo

    wuqa, tana can gida a kwance

    Mal. Salisu ya dauki salati, kafin ya ce.

    “Wacce yar tawa daga ciki Hajiya?”

    Ta ce, “Zulai”.

    Ya cc, “Don Allah kiyi haquri Hajiya, insha Allah

    zan ja mata kunne daga yau ba za’a sake ba,

    kiyi-hakuri”. _

    ‘ Kaka ta cc, “Ainazone don in sanar da kai, don

    wallahi kotu zan kai ku, don ni ban hada jika da

    kowa ba. don haka duk Wanda ya nrmi takurawa

    marainiyar Allah to kotu kawai

    za ta raba ni dashi

    ..Mal Salisu ya ce, “A’a, kar ki haka, don Allah

    Hajiya kiyi haquri, insha Allah ba za’a » sake. Ba.

    Zanje yanzu ma in sameta, wallahi sainaci

    mutuncin ta zanja mata kunne.

    ‘ Kaka tace To taci, albarkacinka , ”amma wallahi

    ka fada‘ mata kada ta sake”. “

    Ya ce Insha Allahu”.

    Sannan ta juya ta tafi kai tsaye gidan su Rakiya

    ta nufa tai sa’ a kuwa Rakiyar na zaune ‘a tsakar

    gidan ita da uwarta Kaka tace, “.Suwaiba. wurinki

    :naxo ki jawa ‘yarki kunne akan Jikata wallahi

    idan har suka Kara dukar min ‘ya to fa kotu ce

    zata rabani , da ku don ba zan lamunta ba”. .

    ‘ Suwaiba ta ce, “Kaka idan kin gadama daganan

    ki wuce kotunma, ki tati kon woli, amma.idan

    Rukayya ta Kara dukan Rakiya, nace su rama

    suyi mata’ dukan tsiya. inga.tsiyar: daure mata

    gindin da kike yarinya zata zauna ta addabi

    Kowa a gari

    ‘ Kaka ta ce, “Oh, ashe ma ke kika

    ’ sa su dakarmin ita kenan. to da kyau ‘ki saurari

    _ sammaci

    Suwaiba tace ba sammaci ba ‘falwaya ma ubanta

    Nimafa da kike ganinanan ba qaramar tantiriyar

    ‘yar iska bacr, babu wanda nake tsoro duk garin

    nan don kiji“. ‘*

    Kaka ta’ce, “La ila ha iilallahu! Yanxu suwaiba ni

    kike zagi saboda ‘yarki’?”

    “Saita fashe da kuka ta fice daga gidan wai an

    Zage ta Tun daga daki *Abubakar ya jiyo ta, ya

    mike ya fito a hasale sukai karo a zaure, ya ce.

    Ya aka yi ne kuma Kaka?“ . Cikin kuka tace,

    “Kyale ni Habu, wai ‘ yau ni cc Suwaiba ke zagi‘

    Kiri-kiri ba kunya Abubakar ya ce “Suwaibar

    Kaka? Anya. kuwa‘?“ ‘ , “Karya nake Habu, ai

    dama na saba,to nai maka wadda na saba”.

    Yace”Ni fa ba haka nake nufi ba, kaka baki

    fahimceni bane” Ta ce; “Gafara can, wallahi idan

    baka Je ka ramo min zagin da taiminba allah Ya

    isa wallahi” Abubakar yai murmushi kafin yace

    “T0 daina kukan haka nan, zan je in ramo miki

    yanzu, shige cikin gidan”

    Ya samu ya ‘lallaBata ta wucc cikin gidan,

    sannan shima ya shige dakinsa. Yana gamawa

    ya fito ya kulle dakin ya kwallowa Rukayya kira

    yana daga zaure, tana fitowa ya bata Naira darin

    kalaci sannanya ficce ya tafi

    wurin aikin sa.

    ::::::::: :::::::::: :::::::::::::

    Babbar sallah ta kusa, don haka duk hada-hada

    ta koma ta shirye-shiryen sallah, .kowa ka gani

    ta yanda zai yi ya samu ya tafiyar‘ da ‘ya’yansa

    da iyalinsa yake.

    ‘ Abubakar tunda wuri ya samu yai musu siye-

    siyen sallar su tun daga shi kanshi har‘ Kaka

    zuwa’Rukayya, hatta kudin dinkin ya . biya saura

    na Rukayya kawai.

    , Kullum‘ sai ‘Kaka tai masa mitar dinkin Jika,

    tun yana sharewa abin har ya soma isar sa, gashi

    yana saura kwana hudu sallah,kuma har yanzu

    ba ai masu albashi ba.

    Don’ haka Abubakar ya nemi aron Naira dubu

    wurin abokinsa, yana dawowa gida k0 dakinsa bai

    shiga ba ya nufi dakin Kaka. Tans zaune ita’ da

    Rukayya suna cin abinci, Abubakar ya ce

    Yau dai’na fita Kaka, ga kudin dinkin wannan

    mummunar da ake ta yi min mita kullum, na huta

    da ciwon baki_

    Kaka ta dauka tana fadar, “To ka kuwa kyauta,

    amma da har na fara tunanin k0 in siyar da dan

    maraqina in amso mata dinkin nata,dashine don ‘

    na dauka baka da niyyar amso mata”.‘

    Abubakar yace Hmm! Kaka kenan, ai gashi nan na

    ranto nabada, na huta . ’ Ya wuce zaure abinsa

    ya shige dakinshi.

    Rukayya ta warci dubun tana tsallen’ murna,

    tace.

    “Kaka baje na karbo?‘

    Ta ce, “Jeki ki karb0 abinki kiyi sauri, ko

    Yan iskan yaran garin nan sun tsokane ki kar ki

    kula su“.

    Ta ce, “To kaka”.

    Ta dauki hijabinta tana tsallen murna ta fice.

    Tana shawo kwanar gidansu ta hango yara sunyi

    dandazo ana ta kade kade jikin Rukayya har ciri

    yake ta nufi wurin, inda ake_ ta ihu, “Ga ‘yan

    kura. ga ‘yan kura masu wasa da kura)” sai a

    kwasa aguje ayi nan riii, ayi nan rii

    Rukayya ta samu abinda take so, ta ma ~”mance

    da aiken da akai mata, ta rufawa sauran yara

    baya suka shiga bin masu wasa da kura, sai da

    suka zagaye garin kaf.

    . Ita da aka aika tun wurin la’asar amma har

    duhun magariba ya keto babu ita babu labarinta.

    ‘Hankalin Kaka ya tash ta leqa dakin Abubakar ta

    kwalla mashi ‘kira, ya fito yana fadar.

    “To wani abin ne kuma k0?”

    Kaka ‘tace tunda fa na bawa Rukayya kudin

    dinkin nan taje ta karBo har yanzu bata dawo

    ba”. .

    Ya ce”To sai me Kaka? Idan ta bata ba mun huta

    ba, kema kin zauna bakin ki ya huta”. Cikin

    rikicewa ta ce, “a bakin ka ba mara mutunci me

    bakin tsiya, bari inje ni na nemota dukma indata

    shiga”. _ Tai waje tana mita, Abubakar yai

    murmushi wanda iyakar sa saman laBBan sa, ya

    koma dakinsa ya sanyo rigar sa ya fita ya ja

    gidan ya nufi hanyar neman ta, duk inda ya ga

    dandazon yara sai ya je ya duba amma babu ita.

    Yana Shawo kwanar gidan Maigari ya hango dan-

    dazon yara suna bin ‘yan kura. ‘Tabbas tana nan

    ciki”. ‘ _Abinda zuciyar shi ta ce mashi kcnan, ya

    shiga kutsawa yana neman ta. Can gaba-gaba ya

    hangota ita da wata yarinya suna ta rabzar fada,

    sai qokarin raba su ake sunqi rabuwa, da alama

    ta sami ‘yar masifa irinta. Abubakar ya kutsa ya

    riqo hannunta, tana ganinshi kuwa ‘yan cikinta

    suka rikice, idanuwan nan suka yo war waje.

    Yanda ya riqo ta haka ya rinwa janta har” gida

    ya hankada ta tsakar gidan, Ya dauko igiyar guga

    ya shiga zabga .mata tana ihu. . Bai ji shigowar

    ta ba sai dai yaji kukanta. “Kashe ta zaka yi?

    Jama’a ku taimaka, zai kashe marainiyar Allah”.

    Tana ganin kakar ta kwasa aguje ta rugungumeta

    tana ihu, kaka tace

    “Cewa naika kirata ka duke ta? Ba ‘ccwa nayi ka

    nemo min ita ba?” ‘

    Cikin takaici Abubakar ya cc, “Duk abinda

    yarinyar nan~ke yi duk laifin ki ne, ke ke lalata

    ta. Wallahi indai ni zan ci gaba da saka hannuna

    a cikin lamarin wannan to wallahi dole ne in

    hukunta ta tunda dai ita haka Allah Ya yi ta bata

    jin magana k0 miskala . zarratin, kuma harda

    hadi da kin shagwaba ta,

    kinsa ta raina kowa, bata .ganin kowa da

    mutunm, to ni dole na hukunta ta wallahi” “Ina

    Naira ta dubu‘?!”. ‘ ‘

    Ya daka mata tsawa, tai saurin sakin kaka tana

    lalube-lalube a jikinta, har’ da su kwance kallaba

    tana dubawa.

    Abubakar‘ yai murmushin takaici kafin ya ce, “Kin

    yar k0? Da kyau, kinwa kanki don wallahi tallahi

    sai dai kiyi sallar haka, fada kuma kar ki fasa, ki

    tayi, ban ce ki daina ba”.

    ‘ Ya yar da igiyar gugan ya wuce dakinshi

    abinshi. Rukayya ta kara fashewa da kuka, “Na

    ‘ yar da kudin Kaka wurin kallon’ yan kura, bari

    inje in dubo”. ‘

    Kaka ta ce, “Ya za ai ki gansu Jika? Ai ba za ki

    gansu ba, kiyi hakuri kawai in lallaBa shi ya Kara

    miki”. .

    Cikin kuka ta ce, “Ai ba zai Kara min ba”. .

    Kakata ce, “Ya. ma isa? Share hawayen ki, ki na_

    zaune sai ya kara su k0 da ya rantse sai dai ya

    yi azumin kaffara”.

    Rukayya ta share ‘hawayénta tabi kaka dakinta

    tana fadar.

    “Dubi, inda ‘duk ya ji min ciwo, wallahi yana

    tafiya sai na rama a wurin ragunan sa”. ‘

    Kaka ta ce, “Shcgun ragunan ma da . kullum ke

    ke dawainiya da su amma bai gani, kullum ya

    kama ki yai ta duka. Wata rana sai na baSu

    shinkafar Beta sun Ci sun mutu inga ta tsiya,

    kema ki hula. Allah Ya ‘soki ma an kusa kwashe

    su ki sami sauki”

    Rukayya ta ce”Shinkafar Bera ita ke kashe su

    Kaka?”

    Ta ce”Sosai ma, ai k0 ke kika ci sai kin . mutu ba

    raguna ba”. *

    Rukayya tai shiru zuciyarta na saqa da

    warwara.

    Kaka tace, Tashi ki dauro alwala kiyi sallar

    magariba”.’ ‘ ‘

    . “Bata ce Kala ba ta miqe ta nufi wurin da . ake

    ajiye butoci ta dauka ta nufi kewaye

    Ana gobe daren sallah Abubakar ya karbo

    dinkunan sa dana Kaka ya kawo mata yana nuna

    mata.

    Rukayya na kwance saman gado tana kallon su,

    dinkunan shi kala uku, na Kaka kala

    biyu. .

    Sai data gama ganin nata sannan ta ce.

    “Ina na Jika?” ‘ .

    Ya ce ”Wacce Jika Kaka? Ai na rantse tunda ta

    zubar da kudin wurin fada ba zan qara fitar da

    wasu in bata ba, wallahi sai dai tai

    sallar haka”. _ ‘ Kaka ta jefa mashi nata, “Ai ko

    indai ba _zaka amsowa Jika nata ba to nima ban

    so, wallahi sai dai ka hada duka ka rike”. ‘

    Abubakar ya ninke kayan da ta jefa masa suka

    zube qasa, ya ce_

    “Ba zan tafi da su ba, sai dai in kinji ‘ haushi ki

    kyasta masu ashana su qone, koki bada sadaka

    duk daya wai makafi sunyi dare, kinga tafiya ta”.

    Ya wuce abinshi ya bar mata kayan

    Rukayya ta fashe da kuka tana harbeharbe da ta

    tabbatar ya tafi Kaka ta ce, “Ke yi shiru Jika, ai

    dama so

    yakc ya‘ sa ki_ kuka, idan kika yi ai kinga yai

    nasara Ki kyale shi dole ya amso miki dinkin

    Inma bai amso ba sai ki saka wadannan nawa

    Tana kukan Rukayya ta ce, “Wadanne zan saka?

    Wannan dinkin tsaffin su zan saka?

    Allah Ya sauwake” . ‘ Kaka ta ce, ”Ba sai ki ba da

    su a rage

    miki ba?” Ta ce, “Allah Ya sauwake ni dai ban son

    su, nawa nakeso”. . Kaka ta ce, “To kiyi shiru

    haka nan

    muga iya gudun ruwan sa”.

    Ta samu da kyar tai shiru,“ amma zuciyarta na

    mata sake-sake kala-kala. . ‘ ‘ ‘ Cikin dare duk

    sun‘ kwanta barci amma Rukayya ta kasa barci

    saboda tunanin rashin kayam sallah, ta tashi

    zaune tana tunanin abinda zata yi itama ta‘

    guma masa. Can ta tuno’da

    shinkafar bera da Kaka ke ajiya a karkashin gado

    saboda Beran dake matsa masu.

    Ta lallaBa ta dauko ta tamkar wata munafuka, tai

    sadaf-sadaf ta fita waje ta sami kwano ta zuba

    shinkafar ta zuba ‘ruwa ta lallaba ta nufi wurin

    ragunanshi. Duk sun ma yi bacci,‘ ta girgiza

    gudayana motsawa .ta miqa mashi. Kamar jira

    yake ya kafa kai ya sha sosai.‘

    Ta nufo gudan tana girgiza shi, yai kuka

    “Beyyy!‘ tai mugun tsorata ta zubar da ruwan. ‘

    ta ruga daki aguje ta kudun dine saman gado.

    K0 minti biyar batai da kwanciya ba taji ragon ya

    soma dire. dire, Abubakar ya fito daga . .dakin shi

    hankalin shi tashe, ya kwance ragon yana duba

    shi. ‘

    Ragon ya fadi yana harbe-harbe, Abubakar ya

    rude yai dakin Kaka aguje ya tayar da ita yana

    fada mata rago ba lafiya, ta rude sukai waje. .

    A lokacin har jikin ragon ya saki, sai kumfa da ke

    fitowa daga bakinsa.

    Kaka ta ce, “Maza dauko wuqa ka yanka shi,

    gazawa zai yi”.

    Abubakar ya juya ragon ya kalli gabas, ya ce

    “Bismillahi, Allahu Akbar”. Sannan ya yanka. ,

    Jikin Abubakar ya mutu saboda gazawar ragon

    nasa, duk cikin ragunan yafi kowanne girma, Naira

    dubu hamsin sukai cinikin sa gobe za a zo a

    dauka. Don haka babu wani kuzari a jikinsa ya

    tafi daki ya kwanta, sai dai batun barci babu‘

    labarinsa, ita kanta Kaka sai data dau lokaci kafin

    baccin ya dauke ta.

    Rukayya k0 dadi ne dankare a zuciyarta, tana

    labe tana kallon su. Yanda ta ga Abubakar ya

    rude sai yai nan aguje ya dawo nan aguje dariya

    kawai take masa har da rike cike, ta rufe’ baki

    don kar wani yaji ta.

    Tunda sanyin safiya Abubakar ya tashi ya tafi, ya

    kira mahauci don ‘siyar masa, gashi ranar sallah.

    Tare suka dawo da mahaucin, ya duba ragon yai

    masa kudi dubu ishirin.

    Babu yanda ya iya haka ya ce ya bayar, a take

    ya kirga kudin ya bayar sannan Abubakar

    ya tafi dakin Kaka ya fada mata yanda aka siya

    Kaka ta ce ”Anya Habu ragon nan bai mutu ba

    aka yanka?” .

    Abubakar ya ce, ”Kai Kaka, Allah Ya sauwake, sai

    kace dai ba Musulmi ba zan yanka mushc? To ko

    da na yanka shi sai da ya harba, yanzu inda

    gabansa kika fadi wannan ai kinga ba zai siya

    ba”.

    . Kaka tace, ‘A’a, ai nidama ban sone ka aikata

    abinda Ubangiji zai yi fushi da kai ne’ .

    Abubakar ya ce, “To bai mutu ba na

    yanka, yanzu ma buhu zaki ara mana zai fede

    anan.

    Kaka ta ce, “To bari in duba maka” .

    Rukayya ta mike simi-simi ta raba Abubakar ta

    wuce tamkar wata tsohuwar munafuka, ta nufi

    wurin mahaucin tace masa ‘ “Baba ragon nan sai

    da ya mutu aka

    ‘ yanka shi, kar ka siya”.

    Mutumin ya zaro ido yana mamaki, kamin yai

    magana tai saurin rugawa daki abinta ta

    haye kan gado“ Kaka ta zakullowa Abubakar buhu

    a

    Qarqashin gado ta bashi, ya fito. “Yauwa ga

    buhun Baba Halliru”. Da

    yake haka ake kiransa a garin. Ya ce “Riqe shi

    nan wurinka Abubakar,

    bani kudina”. Gaban Abubakar yai wata irin

    faduwa,

    ya ce

    “Saboda me Baba?” ~

    Ya ce “Saboda ni ba mutumin banza bane irinka

    da zan siyi mushe in saida wa al’ummar

    Musulmai. Ba

    “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un! Baba wallahi ba

    mushe bane, ni na yanka shi da hannu na

    wallahi”. ‘

    Ya ce”Kai kaga ni dai ba abokin wasanka bane,

    ka bani kudina kawai ban siye na fasa Kanwar ka

    da bakinta ta fada mini mushe ne ka yanka. wato

    ga mutumin banza ko

    Idan bakwason wannan littafin kuyi magana mu

    canja

     zallah shared a profile .

    0 Comments

    Heads up! Your comment will be invisible to other guests and subscribers (except for replies), including you after a grace period.
    Note
    error: Content is protected !!