Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
    ………….””Har Zuwa Ranar Suna Kullum Malika sai taje gida,in Saleem zai Fita office Tare suke Fita ya sauketa shikuma ya Wuce,Daga Hajiyar har joda sunji dadin Haka sosai,Yan Malumfashi sunzo mota biyu,mota daya daga barayin Dangin Baban Joda,daya kuma Daga Family dinsu Hajiya,wato Baffanin Malika kenan,hakama yan kumo sunzo duba bby,Sun kuma zo da Abun arzikisu sukayi barka suka koma.

    Ummi ma tazo,Da kayan suna Niki niki da nata dana Abbi dana ya marwan Wanda dama joda tazo da duka kayan Suna na bukatan da suka siya na haihuwa,sai kuma ya Turama Ummi kudi ta kara mata,Abun fa masha Allah sai wanda ya gani Ya marwan yazo kwana daya yayi ya koma inda yayi ma yaro Huduba da *SALEEM* wato yama Acp takwara kenan jin wannan Suna yasa daga Saleem din har Malika sukayi bajinta ban girma Malika makullin mota sur tabama Joda Shiko Saleem Kudi ya bata 100k ita kuma Malika ta dora mata Nata darin akai making 200k,Joda Saboda murna sai da ta Rumgume Malika kamar ta mata kwallar saboda godiya,Hakama Hajiya tayi ta godiya,itako Malika tace don Allah su bari,miye amfanin uban Dukiyan datake dashi in har batayi ma nata ba.

    Saleema ma tazo Ranar suna ta kwana ita da malika sai washegari ta koma Abuja ta kwana kafin ta Wuce,Taro ya tashi lafiya sai Fatan Allah yara young Acp,wanda suke kira da Junior.

    Hajiya ce ke Kula da Maijego da danta cikin kwanciyar Hankali,Hakama Malika itama tana cigaba da kula da kanta da kuma Mijinta da kuma ya”yanta,hakama Shima Saleem yana iya Bakin kokarinshi na ganin ya Sauke dukkan Hakkin Malika da na ya”yanshi daya Rataya awuyanshi,game da Harkan kasuwancinta Shi Malika ta dora Amatsayin manajojin kamfafoninta,duk wani kudi da zai Shiga ko Ya fita,ko in wani Abu ya taso,sai dai in Abu ya gagareshi sai ya Fadama Malika ita kuma amtsayinta na wacce tasan kasuwanci sosai sai ta Fitar da mafita cikin Lokaci,Shiyasa Kasuwancinta da Kudinta suke kara hauhauwa.

    Mganar koyamata Mota kuwa ya cika alqawari Duk Ranar Asabar da lahadi suke Fita da la”asar yana koyamata mota dayake Malika akwai kwalkwalwa basuyi wata ba ta koyi mota sosai,har tana tuka kanta taje gidan Hajiya ko asibiti,ammh bata taba Tafiya mai Nisa ba,sai dai ko cikin gari in zata Fita.

    Joda kuma ta cigaba da jegonta cikin kwanciyar Hankali ayayinda Da hajiya ke kula da ita,bata koma ba sai tayi wajen wata biyu,taje Abuja ta kwana biyu taje malumfashi ta kwana biyu Shima,har wajen Malika tazo ta kwana,Washegari mijinta yazo ya dauketa suka je Abuja suka kara kwana daya suka daga zuwa birinin na ikko da su da Little Acp dinsu wanda yayi kiba sosai yasamu Nonon uwa mai kyau da kuma kulawa in ka ganshi gwanin ban” sha’awa.

    Saleem ya saka Ayda awata private,sch Bby clss,saboda bakinta ya bude sosai ga Shigen wayau shiyasa Saleem ya sata amkaranta bakinta yakara bude achan,Malika ke kaita watarana taje ta ta Dauko Watarana kuma Saleem ya kaita kafin ya Wuce office in ko ya makara sai ya barta Malika ta kaita,Abun nasu cikin kwanciyar Hankali gefe daya kuma tana cigaba da Renon yan biyun ta suma da suka habake sukayi kiba sosai sai da wannan karon goyon Rigimammu take,don su Aryan akwai Rigima da daya ya Fara kuka,toh Daya zai dauka,Haka take Fama,don ma su merry suna kokarin Taimakamata da Renonsu wani lokacin.

    *

    Zahra ta yi sanyi Fiye da yadda kuke Tunani ta chanza daga zahra ada ta koma Fatimatulzahra’u Wacce take da Tarin natsuwa da hankali yanzu ba wannam rawan kan,da kuma shigen iyayi bashi,Game da zafin kishinta kuwa ta Fahimci Halittanta ne,sai ta koma tana Rokon Allah ya rage mata wannan Zafin kishin,kuma Alhamdullah,Yamzu Abun ya fara ragewa ba kamar da ba.

    Auren Nadira shiya kara maidata wani so silent,ada ta saba komai tare suke koda suka rabu da Saleem,kewar batamata yawa saboda Tana ganin Nadira ko banza zasu kwana tare su tashi tare,toh yanzu Nadira tayi Aure tana gidan Mijinta tana zaune lafiyanta,Ta kwantar da Hankalinta Da Zahra Taje gidan tayi mamakin ganin kibar da Nadira ta narka ya”yan Mijinta kuma shashenta suke Wuni Suna Anty kaza zanci ita kuma tana ta Ina kasa dasu,shiyasa ta Shiga ran iyayen kunsan me da wawa,Kwata kwata suna tafiyar da kishinsu Cikin tsafta Domin kunsan ba inda ba”a kishi sai dai akwai masu na ilimi dana Jahilci,Zahra bata fahimci Nadira nada ciki ba sai da ta sanar da ita da kanta tace mata tana ciki na tsawon wata Hudu,Abun ya daki zahra haka ta koma gida ta kulle kanta adaki tana kuka,Tana kara Nadamar Abunda ta aikata da”ace ta kwantar da Hankalinta da yanzu kila ta haihu Bama daya ba,ammh gashi har Nadira tayi aure jiya jiya har ta samu ciki,haka dai ta kwana kuka ta kuma yi alqawarin maida al”amarinta ga Allah ko zai kawo mata mafita.

    Momi tana iya bakin kokarinta wajen ganin Zahra ta saki ranta ammh sai ahankali Shiyasa ta Shirya musu Tafiya lagos wajen Hajiya baraka mahaifiyar Su Nadira,Zahra taji dadi sosai Balle ma hajiya baraka macece mai Fara”a da barkwanci Shiyasa Zahra ke jin dadin zama da ita,sati daya Momi tayi ta baro Zahra chan ta dawo kuma ba laifi zahra ta saki ranta dayake ta sake aure bayan Rasuwar Mahaifinsu Nadira,har ta haihu,Zaman lagos yayima Zahra dadi sai tayi wata biyu kana ta Biyo ya Nadir suka dawo tare wanda Suka isketa achan Shida matarshi Sati daya sukayi da zasu dawo da taboyosu.

    Bayan dawowarsu ne Ya Nadir yazo har gida ya samu momi ta complain Din zaman da Zahra take haka babu Abunda takeyi,gashi yaga Duk ta rame ta koma kamar Zahra bukar Mada,momi tayi bayanai ta yi iya bakin kokarinta ammh Zahra sai ahankali ganin haka yasa yasamu Abba ya mai mgana zai Nema ma Zahra aiki saboda zaman kadaichin yayi yawa,Bai yi mai musa ba,shiyasa ya karbi Takardunta bata da masaniyar komai sai da gidan Redion Freedom kano suka kirata interview Shi da kanshi yazo ya dauketa ya kaita tayi interview,cikin Nasara ko sati batayi da zuwa suka Turo mata sakon Sun Dauketa aiki ashashen labru,murna wajen Zahra ba”a mgana Haka ta Rumgume ya Nadir tana murna momi da Abba suna dariyan Farinciki Domin rabonsu da ganin murnan Zahra haka Har sun Manta Arana.

    Ranar data Fara Zuwa aiki Ranar Ya Nadir ya bata key din sabuwar motar daya Siya mata 4matic,mai kyau,Zahra kamar bakinta zai Tsage saboda godiya,hakama su Abba da momi suna mai godiya ya bata rai yace Haba Zahra fa yar”uwanshi ce saboda haka zai iya komai domin ganin Rayuwarta ta dawo kamar da,Haka ko akayi acikin Sabuwar motarta tafara Zuwa aiki Ranar,Data tashi kuma ta biya gidan Nadira ta nuna mata Sabuwar motarta itama Nadira tayi murna haka suka Rinka Dane motan suna Santi,ita kanta Nadira murna ya kamata ganin Zahra Ta chanza kamar ba ita komai yanzu tana yinshi cikin aji ne,ganin Zahra ta Shirya zata tafi tace mata zata biya gidan Ya Nadir,aiko Nadira tace sai taje Dr ta kira awaya tace mai zata gidan Ya Nadir ita da Zahra yace adawo lafiya,saboda kwakwa Nadira ita tayi Driving dinsu zuwa gidan ya Nadir suka kuma yi sa”a suka iskeshi agida nan Nadira ta sakamai kukan wlh itama sai ya Siyamata mota,Yako yace bazai siya mata ba taje mijinta ya Siya mata nan ta bare baki tana kukan Shagwaba Zahra da matarshi wacce suke kira Madam suna mata Dariya sai yammah Zahra ta maidota gida suna tafe suna Hira Nadira na kara Yima Zahra Nasiha da kuma hakuri da Rayuwa Zahra ta mata alqawarin insha Allahu ta chanza ita yanzu ko me mata Uku ce itace ta Hudu yazo ciki zatayi dashi ta gaji da zaman gida,Don ma dan aikin nan da Ya Nadir ya samo mata shike Debemata kewa ammh Kadaichin yayi mata yawa Sosai,Dama haka Rayuwa take Duk wanda baiyi Sharar masallaci ba to ai zai yi na kasuwa kodon Dolensa don Ubanshi..”

    Dalilin wannan Abun yasa Shakuwa tare da Tsantsan Damuwa da juna ta Shiga tsakanin Nadir da Zahra,shi duk a kokarinsa na ganin ta dawo Normal zahran ta kuma Alhamdulillah yabada Gudumuwaa domin ko Zahra bata dawo duka ba,tafara dawowa sai dai yanzu wannan Zahra ta gama Daukan Darasin Rayuwa sosai kuma ta kara gogewa da wayewa ba kamar da da bata wayau sosai ba,yanzu Saboda Cudanya da jama”a yasa idonta ya bude Sosai ta kuma gane Rayuwa.

    Wannan Shakuwarsu nasu ita iyayensu ke kallo da makusantansu suke zaton suna soyayye ne,kuma ba Haka bane,Kawai kulawa ne da kuma Shakuwa,hatta Matarshi ta Fara Shaka da Zahra shiko ko ajikinsa bai maida kai ba,hatta Nadira tana ta addu”an Allah sa Ya Nadir ya auri Zahra da tafi kowa murna Har Ummah su ta kita ta tsegumta mata itama Tayi murna Sosai bata kuma jira komai ta kira Abban Zahra ta sanar dashi wanda yaji mganar abazata Duk da dai Shima yana ganin Shakuwarsu ammh ko da ya tambayi momi sai tace batajin akwai wani Abu atsakaninsu,Ammh jin Batun Umman lagos yasa yace zai Nemi Shi Nadir yaji..

    Koda ya kira Nadir ya zaunar dashi yana Tambayanshi shi ya kira Umman lagos yace yana Son Zahra,mamaki ya kama ya Nadir yayi Shuru yana hasaahen Daga ina wannan mgnar ta Fito ganin yadda yayi ne sai Abba yace kada ya damu in ba haka mganar take ya sanar dashi,girman Abba a idonshi da kuma Kimarsa da Yadda yake arayuwarsa yasa yakasa masa musu ya amsa da eh shi ya kirata ya sanar da ita,jin haka yasa Momi da Abba sukaji dadi sosai har suka kasa boye murnansu Afili,Shiko Ya Nadir zahra ya kira ya Fara tambayanta itama taji mganar tayi mata bazata Tace itama bata sani ba,sai da ya kira Umman lagos yake tambayanta ta kyalkyacemai da Dariya tana gayamai yadda sukayi da Nadira tace taga ya tsaya kunya Shiyasa ita ta kira baban nashi ta sanar dashi kada wani yamai Shigar Sauri,ganin yadda gabadaya lamarin ya Daure Nadir shiyasa ya share bai nuna ma kowa bai ta ma Zahra kallon Wacce zai ya Aura ba yana kallonta ne da Sigar dayake kallon Nadira,ammh kuma Abba ya Wuce haka agurinsa bazai taba watsamai akasa a ido ba,Zai auri Zahra koda baya sonta ai kanwa take awajensa..

    Tunda Abun na gida ne Umman lagos ne kadai tazo aka sanya Rana wata biyu masu Zuwa sai lokacin Ya Nadir ya sanar da matarshi,Taji wani iri sosai kuma bata iya boye kishinta ba,harta koken ko don bata taba Haihuwa ba yasa zai kara aure,lallashinta ya shiga yi da bata bKi har ta sauko ta karbi mganar hannu bibbiyu ta kuma yi mai Fatan alheri Duk da kishin Mijinta na cinta ammh ta danne Tunda dai mijinta bai Chanza mata Daga Son daya ke mata,Sai dai Wani dan Abunda ba”,a raasa ba Tunda Dan adama ajizi ne Tara yake bai cika goma ba.

    Zahra ma haka taji Abun kawai Daga sama,Ammh kuma akasan Ranta tayi murna Domin Shima ya Nadir Namiji ne,Kodai baikai Saleem ba to zata jerasu a Aji da Takama da isa,lokacin daya Fara zuwa wajenta da Sigar Mijin da zata aura yayi mata mganganu sosai ya kuma sanar da ita sai tayi Hakuri don yana mata kuma ta sani,so suyi Hakuri da juna duka sai su zauna lafiya,Zahra bata daukan ma kanta Tun Farko ba,tuni ta watsar da wani kishin Banza ta rike Sabon Mijinta kuma yayanta dakyau gefe daya kuma suna ta Shiryen Shiryen bikinsu,da farko ita fara wasan buya da Madam,sai da bita har wajen aikinta bayan ta dawo daga asibiti tana mata tsiyan haka zasu kwashe In ta Shigo ai an zama daya,Zahra tayi murna sosai nan da nan suka koma kamar da,wani lokacin in Zahra tatashi Daga wajen aiki ta kan biya,Nadira kuma ta fikowa murna kamar me,tana ta addu”a Allah yasa kada ta Haihu sai bayan biki cos tana son ta baza kara”i ne part 2 awannan karon.

    Biki ya karato Duk da ba gayyah Zahra tayi sai yan wajen aikinsu kawai sai wasu daga cikin kawayensu da sukayi mkranta Zahra ce ta matsamata ta kira Saleema ta Sanar da ita zatayi aure,bata yi musu ta karbi lambarta ta kirata sai da ta sanar da ita Sunanta kana ta ganeta Saleema tayi mamaki sosai kuma tayi murna da jin Zahra zatayi aure,nan take Sanar da ita Tayi Nauyi ammh zata Roke Ya Sadiq in ya yarda zata zo Katsina ta kwana sai su taho tare da Malika,jin haka yasa Zahra tace ta Rubuto mata Full address din gidan Saleem da lambar wayar Malika nan ko take Saleema ta tura musu suka rabu cike da Farinciki kowa na Mamakin yadda dan”uwansa ya chanza wai Saleema keda ciki wai Chanchadi😂

    Nadira tabama Zahra Shawaran taje Har katsina ta kaima Malika Katin biki da cimgam,da kuma nemam ya Fiyan juna Tunda yanzu komai ya Wuce,Zahra ta yarda da mganar Nadira hakama momi ta amince mata taje,domin itama tace zata kira Ummi ta sanar da ita Ranar bikin,Nadira ta so ta raka Zahra ammh sai Dr ya hana Don cikinta ya tsufa,Shiyasa Ana saura kwana goma biki Zahra ta Tafi katsina da kanta ta tuka kanta cikin Sabuwar motarta ammh sai da ta tambayi ya Nadir ya kuma bata dama.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!