Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    ……………”Su Maman Abba da Saleema su kadai aka bari suka cigaba da soye soye basu Tafi ba sai da komai ya kammallah,Suka taimaka aka gyara gidan kana,maman Abba ta Wuce zamfara ita kuma Saleema tatafi Abuja ta kwana Washegari zata bi jirgi Zuwa Abia.

    Ita kuma Hajiya, Ummi ta roketa Kan ta Zauna ta dan kara ko Sati daya ne kafin goggo Hadiza tazo wacce tatafi minna An mata rasuwa,sai ta dawo kana zata zo ta zauna Da Malika uwar mazaje.

    Hajiya ta Zauna da Malika har Na tsawon Sati biyu tana kara kula da ita da Kuma su Ayyan Duk da gasu Merry suna kokarin Taimakamata,sai Ranar ta cika kwana ashirin da Hudu kana goggo Hadiza tazo,sai Hajiya Ta koma gida ta barta tana Kula da Malika wacce ta warke kamar ba ita ba.

    Tun Malika na kwana 36 Da haihuwa jini ya Dauke mata tayi wanka Tafara Sallah Ammh Bata bari Uban gayyah ya sani ba,domin taga take takenshi so yake ya barta da Abun kunya agaban Goggo Hadiza,Don Tun Satin daya wuce yake damunta da ya kosa ta Fara sallah wlh a daddafe yake yayi kokari ta taimakeshi,Bata nuna mai komai ba,Sai Ta nuna mai Data Fara zata mai mgana,sai dai wani lokacin ta Saci jiki taje dakinsa ta Dan mai Dubaran,su na mata ammh Duk da haka bai wani gamsuwa shi burinshi yajishi Cikin babban Fada😂.

    Ga wannan karon su Ayyan da Bala”in kuka suke da Tsotse,bata da lokacin kanta,data samu sararin zuwa dakinsa ko Dadewa baza tayi zata ji kukansu da kuma kiran goggo Hadiza,Da kuma ta Fahimci Dakinsa Taje Sai goggo Hadiza ta kama mata Fadan zatayi kazantattacen jego matukar ta biye ma Namiji kaita zai yi ya Rabo wlh,wato yaga jiki yayi Taushi ,shine ita zata biyemai Shiyasa wani lokacin ko ya kirata bata Zuwa,sai tace mai su Aryan na Rigima.

    Yau da Wuri ya dawo yana Shigowa Direct dakin Malikan ya Shiga,yana Shiga ya ganta tana sallar mangariba,,galala ya tsaya yana kallonta,yana mamakinta domin Jiyan nan ya Tambayeta yaushe zata Fara Sallah ,tace bata sani ba,akofar dakin ya coge yana binta da kallo itako ta jikin madubi ta hangeshi sai da gabanta ya Fadi,Sai ta Daburce ta idar da sallar ammh sai ta sake kabartawa Yana kallonta bai mata mgana ba, illah takowa dayayi ya zauna agefen gado batare da yayi mata mgana ba.

    Tun tana mai karyar Sallah harta hakura ta Sallame tana Raba ido,bata yarda sun Hada ido ba,tayi zaune tayi Zuru gabanta na bugawa,Ta gefen gado ya kalleta kafin ya saki Siririn mirmishi kafin yace”Kin idar da sallar..? Na zata sai gobe zaki idar..?

    Shuru Malika tayi tana wasa da Gefen Hijabinta,ganin batayi mgana bane yasa ya mike yana Fadin”Ina ayda ko tana wajen goggo ita Da su Aryan..? Da kai Malika ta bashi amsa,Dariya ta kamashi yayi yana Fadin”Kin zama kurma ne..? Ko Azumin mgana kikeyi..? Bata dago ba balle ta bashi amsa,kofar ya isa ya sama key kafin yazo ya Tube karamin Towel ya daura iya kugunsa ya Fada Wanka tana binshi da kallon mamaki,tana zaune awajen har ya Fito yana kallonta Shima ita yake kallo kai Tsaye yace mata”Kinsan Hukuncin macen data kema mijinta karya..? Ya fada yana goge Sumar kanshi da wani karamin Towel,Kanta na kasa tace”Karya kuma…? Dan mirmishi yayi kafin yace”Eh kin min karya kince baki Fara sallah ba,saboda kada Nameni hakkina ki bani ko Malika..? ya Fada cikin wani yanayi,Mikewa tayi jikinta yayi sanyi kafin tace”Wlh ba…”Shiii…Is ok,ai bazan Nema ba Tunda na Fahimci Guduna kike,bakomai Zan zauna ahaka ammh ki sani in na kasa control din kaina har na Fada wani Hali kome ya Faru kece Sila..”Yafada cikin son Tabbatarwa,kafin ya isa gaban Merro ya jawo lotion ya Fara shafawa.

    Jikin Malika yayi Sanyi da azama tataka zuwa gareshi kawai sai ji yayi ta Fadaomai jiki ta kamkameshi ta haya,Hannu yasa yana so ya bambareta daga Rumgumar da tayi mai,ammh ta ki sakinshi suka Fara kokawa,ranshi bace yake Fadin”plz Ki sakeni kafin Raina ya baci,badai jikinki ki keman Rowa ba,ki jika kisha,ni bazan yi zina ba,ammh kisani zan karo wacce ko acikin wani hali na nemeta zata bani kanta..”

    Jin haka yasa ta fashe da kuka tana kara Rikeshi Kamkameshi tayi ta Zuro da hannunta ta cikinshi tana mai Shesshekan kuka cike da Shagwaba,Shuru yayi mata yana bin Fuskokinsu ta jikin madubi da kallo,Kara Hade rai yayi yana Fadin”Wai ina wasa dake ne Malika,i said leave my body ko..?Narkemai takarayi kafin tace”Wlh bazan tashi ba,ni da jikina,kuma Shikenan daga kuskure kadan sai ka yankemin Hukunci baka iya tsayawa kaji Uzurina..”karamin Tsaki yaja kafin ya waigo da karfi ya kuma sa hannu ya Ture malika baya sai ta Fada gefen gado yaraf,Arazane ta dago kanta tana kallonshi kafin ta samu Zarafin mgana yace”Bana son Jin komai daga bakin plz leave me olone,indai kan ki bani hakki na ne,Malika kiyi ta Rike kayanki bazan kara ce miki komai ba Do wht ever u want i dont care..”Yafada kafin ya isa jikin Wardrope ya dauko Wasu Riga da wando na kamfanin Armani,ya saka yayi cumbing din kansa ya Fice bai kara kallon Inda Malika take ba,ta kallon ta bishi kafin ta kwanta bisa gadon Tana Fashewa da kukan takaichi da cin rai,Shiko Ficewa Yayi daga gidan gabadaya,har wajen 10 da Malika taje dakin Goggo Hadiza ta basu Aryan Nono Saleem bai Shigo sai hankalinta ya tashi Zuciyarta ta Fara mata wasu Tunanen ko dai wajen Wata yar iskan karuwan yaje..? Tuni Taji Hankalinta ya tashi,ammh sai tayi saurin Kauda wannan Tunanin Saboda tasan Halin mijinta baya shaye Shaye baya Neman mata,ammh ganin har pass 12 Saleem bai Shigo gida ba,yasa kuma hankalinta yakara tashi tayi Safa da marwan Tsakanin upstair da kuma kasa,haka tazauna afalo tayi Zuru ta Tsurama kofar falo ido,lokacin da 12:30 tabuga ne Goggo Hadiza ta sauko daga sama tana bin Malika da kallon mamaki,itako hankalinta yayi gaba bata ma san goggon ta sauko sai da taji tana Fadin”Malika…”Cike da mamaki…

    Afirgice Malika ta Waigo ganin Goggo Hadiza yasa ta sauke ajiyar Zuciya tana Sosa kanta tace”Bakomai Goggo Zan kalli wani Shiri ne a Mbc yanzu…”Kallon mamaki goggo Hadiza ta Bita dashi tana karantarta kafin tace”Kuma shine kallon atsakar dare malika ..?Kina da danyen jiki,maza ki Wuce daki ki kwanta,dama na Shiga dakinki na kai miki su Aryan ne,sun yi barci kada Su tashi cikin dare suna kuka kinsansu da tsotso..”Kai ta sunkuyar Kafin ta Wuce tana Fadin”Toh Goggo sai da Safe..”Tafada jikinta asanyaye kafin ta haura sama da kallon Tsausayi goggo Hadiza ta bita kafin ta jinjina kai tabi bayanta,ammh tasan Dalilin wannan damuwar ta Malika,ita batajin Shigowar megidan ba Allah yasa lafiya.

    Koda ta koma daki kasa barci tayi wayarta ta Dauka ta latso mai kiran Daidai lokacin dayake zuba hon akofar makeken gidan, nashi megadi yataso ya budemai yana mai Barka da Zuwa shima cike da mamakin yau yallabai yayi dare,duk mai irin aiki irin nashi kowani lokaci zasu iya Fita.

    Sai da ya Daidaita motar a parking space kana ya daga kiran Malika wanda na Uku kenan ya Shigo wayarsa,Tana jin ya daga ta Fashemai da kuka Dan ware ido yayi yana Fitowa daga motar yake Fadin”Meya Abun kuka kuma..? Hmm mata sai abarku ku bata mutum rai kuma ku Fishi nuna ku aka cuta ko..?”Tana Share hanci tace”Don Allah Mallam ka ya Femin,ka dawo gida hakanan Hankalina yaki kwanciya Zuciyata tana Ta Tunanin kila ko kana tare da Wata ne..”Mirmishin gefen baki ya saki kafin yace”Na shigo gida yanzu..”Daga haka kawai ya yanke kiran,jin yace ya Shigo gida yasa ta Fito daga daki da sauri tana kallonshi ya Shigo yana Takunsa cikin isa,har ya hauro saman yana kallonta bai mata mgana ya Bude dakinsa ya Shiga ya maida kofa ya Rufe Ajiyar Zuciya Malika ta sauke kafin ta koma daki tana Share kwallar Daya Tarun mata.

    *

    Har washegari Saleem bai saki ba,,sboda yana Fushi da ita ko karyawa baiyi ba,da goggo Hadiza ta matsamai ya tsaya ya karya sai yace zai karya a office in yaje,kuma Malika na zaune adakin goggon Hadizan daya shigo gaisheta da Safe,Ayda kadai ya daga Data rugo tana gaisheshi ko su Aryan dake hannunta bai karba ba Daga hannunta ya lakace musu hanci yana musu wasa koda Malikar ta gaisheshi dakyar ya amsa kamar yana Ciwon baki ganin haka yasa Malika taja bakinta ta Tsuke ya har Fice,goggo Hadiza ba macece bace mai Shiga Sha”anin yara,kuma Abu na ma’aurata Shiyasa tayi musu bakam kamar bata Fahimci basu jituwa ba.

    Tafi tafi Fushin Saleem yama Malika tsauri wajen Sati daya Abu yaki Wucewa awajensa,gashi yanzu baya zaman gida kwata kwata,baya Shigowa sai around 10 kuma yana Shigowa zai Shige dakinsa ya Kulle,malika tanemi hanyar Sulhu ammh yaki bata dama,shiyasa itama ta Kama kanta,iyakarta dashi gaisuwa sai ko in ya Shigo dubasu Aryan,wani lokacin ma Dakin goggo Hadiza yake tarar dasu,ganin yadda yaki Fahimtarta shiyasa Itama Ranta ya baci da wannan Fushin mara Dalilin da Saleem ya Dauka da ita gabadayansu suka Share juna kowa na ganin Shi ba’a mai Daidai ba.

    Ranar da Malika tayi Arba”in Ranar Ya marwan ya kawo joda gida domin cikinta ya Shiga wata na tara,kuma bashi da wani Hutu,shiyasa ya dawo da ita gida ta Haihu tunda chan kudu ne,koda hajiya ta kira Malika ta sanar da ita cewa kawai tayi zata kira jodan don yanzu bazata ce zata zo ba,kada ta kara wani laifin,Kuma shi Saleem din Ya dauko su daga Airport, Daganan Motar haya Ya marwan ya Shiga ya tafi Abuja achan ya kwana sai Washegari ya hau jirgi ya koma birin ikko don Ba”a bashi Hutu ba wannan ma Excuse ya dauka da zai kawo Joda gida.

    Har Joda tayi Sati da Zuwa ammh kuma Malika bata jeba,Bai cemata ci kanki ba,itama bata tayaba ta rabu dashi,Aranar kuma Yasa ka Direba ya maida goggo Hadiza gida,domin ta matsa zata tafi,saleem ya hadamata Sha tara na arziki hakama Malika tayi ta godiya tana saka musu albarka,Malika ko sai tayi kwallar harta Fadin in goggo Hadiza tatafi zata kara zama marainiya bata da mai kula da ita,itako goggon Hadiza tace Kina dashi mana Malika ga mijinki nan,Cewar datayi haka sai da Malika ta kalli saleem Shiko ya Hade rai kamar bai taba Dariya ba,sai da suka raka goggo Hadiza bakin mota dama Direban gidan Hajiya ne zai kaita,har suka Fice Daga gidan suna daga musu hannu,Shi Saleem yana dauke da Ayda ne,ita kuma Malika Ayyan ne ke Hannunta Aryan ya gama Rigima ya kwanta,Gaba yayi ya barta ita kuma tana Shigowa ta haura sama,Bai Shigo ba sai da Ayda ta tafi wajen su Merry shikuma ya hauro sama dakin Malika ya tarar da ita tana bama Ayyan Nono,Tunda taga ya Shigo Fuskarshi ba Fara”a tace topha,aiko illai gabanta ya tsaya yana Fadin”Miye Dalinlinki na cema goggo Hadiza in tatafi Zaki kara zama marainiya,wannan wata irin mgana ce,sai kisa tayi tunanin ko ina cutar dake ne fa..”Yafada yana mata wani kallo,kanta ta dago tana kallonshi idanuwanta sun ciko da kwallah,,ido cikin ido suke kallon Juna kafin ita tafara Janye idonta Hawaye Datake kokarin Rikewa suka zubomata tasa hannu ta Share Abunda ta iya cewa kawai Shine”Kayi Hakuri..”

    Yadda tayi ne jikinsa sai yayi Sanyi,duk Fushinsa sai ya sauka sausauta murya yayi yana Fadin”Kidaina irin haka ba dadi sai ta dauka wani abu ne..”Kanta na kasa ta dago tana kallonshi tace”Ba karya nayi ba,yanzu kadaina kula dani,Haba mallam takan laifin da nayi bisa kuskure kadan sai ka dauki Fushi dani mai tsawo haka,Sai yanzu nakeji ni Marainiya ce ada,ina ganin ka lullubemin maraicina amhhh..”TaKasa karisawa tayi Kuka taci karfinta da hanzari ya isa gareta ya zauna kusa da ita Ayyan ya karba ya Fita dashi sai gashi ya dawo Shikadai,Hannu ya mikata mata ta karba ya mikar da ita tsaye Habarta ya tallafa yana kallon kwanya idanuwanta kafin yace”waya gaya miki ke Marainiyace,Haba Amanata indai ina raye har abada baki ba kukan maraici..”Yafada Cike da kulawa,Runtse ido tayi hawaye suka kwaranyo mata kafin tace”Ka chanza mallam,ka barni inata wahala da Fushinka..”Harshensa ya sa yana lashe hawayenta,sai da ya lashe kaf,kafin ya Rumgumeta kam yana sakin ajiyar zuciya yake Fadin”Am srry Nayi kuskure insha Allahu baran kara ba..”Yafada yana kamkameta,ajiyar zuciya ta sauke tana zagaye kugunshi da hannuwanta,cikin muryan Sanyi tace”Nayi kewarka Abbu Ayda..”Ta fada tana sakarmai kiss Awuya kamkameta yayi yana Shinshinar Wuyanta kafin lokaci kadan sungama Rikita juna da salon wasanninsu,Cikin Fitan hayyaci suka raba junansu da kayan jikinsu,Kafin su Dangana da kan makeken gadonsu suna Tsotsan juna cike da kwarewa da muradi mai girma.

    Ranar dai ma”auratan komai ya Daidaita tsakaninsu Haka suka kwana manne da juna,don ma Rigimar su Ayyan ta hanasu sakat,ammh duk da haka Sun mori juna ba laifi Saleem ya Famshe kwanakinsa,dama gashi goggo Hadiza ta gyare yarta Sosai Acp ya yaba kuma yayi ta sambatu😂

    *.
    Washegari kuma suka tashi da Lbrin Haihuwar Joda wacce ta haihu lafiya kalau agida,sai da safe Hajiya ta kaita Federal medical Center Katsina,aka duba ita Bby lafiyanta Kalau,Ta haifi da Namiji masha Allah,Dama Malika Ranar take Shirin zuwa sai aka tafi da murna gabadaya,Saleem ya ijiyeta agidan bayan ya Shiga yayi barka Shima ya Wuce office yabar Malika nan sai dare yazo ya dauketa,suna hanyar komawa gida yake sanar da malika zata fara hawa daya daga cikin motocinta da kanta,ammh sai dai su bari Weeked ya dinga koyamata mota,Malika tayi ta murna harda kwallar Farinciki,Abun yayi ma Saleem dadi ganin Walwalar Malikarsa zata dawo,domin shi yanzu babban Farincikinsa yaga Malika na cikin Farinciki akoda yaushe..

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!