Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Karfe 10 da wani abu suka isa anguwan su Malika,wanda Tundaga farkon layin har karshe jerin gwanon motoci ne na gani na Fada,anguwan tacika makil,Malika ko Tunda suka baro Zamfara take kuka har zuka iso katsina,Tun Saleem na bata baki har ya gaji ya kyaLeta.

    Bai samu damar Shiga da motar ciikin haraban gidan ba,sakamakon yadda aka wangale get din Mutane sunyi Dafifi kowa nata daura alwala saboda lokacin Jana’iza ya kusa,Malika dataji kanta na sarawa ta dago kanta tana bin ko”ina da kallo,Zuruf tayi zata bude Murfin motan sai taji hannun Saleem bisa nata ya damke,waigowa tayi tana kallonshi wasu hawaye suna zubomata Kara damke hannunta yayi yana kallonta kai tsaye kafin yace.

    “Kiyi min wata alfarma plz..? Girgiza kai tayi tana Kokarin kwace hannunta,shiko yaki sakinta ganin haka yasa ya Bude baki yana Fadin”kada ki yi kuka sosai,kinga fa Tundaga Zamfara kike kuka,har muka iso nan,don Allah in kika Shiga ciki ki tararro juriyanki kada kiyima Daddy kuka,ayanzu haka yafi bukatar addu’anki Fiye da na kowama..”Runtse ido tayi hawaye suna kwaranyomata kai ta gyada mai alamun taji,mirmishin yake ya saki kafin ya Kai hannun nata bakinshi ya sakarma wani light kiss,kafin ya saketa ta bude murfin motan da hanzari Ta fice tana Rufe Fuskarta da Gefen hijabinta kuka na kwace mata.

    Shi kuma ya Fito daga motan ya nufi haraban gidan inda su Abbi ke tsaye shida sauran yan”uwan Daddy na Malumfashi,gaisawa sukayi yana kara musu gaisuwa,kafin shima ya koma gefe yasamu buta yafara daura alwala domin har an kammallah yima Daddy Sutura ana jiran lokaci ne ya cika a sallaceshi zuwa gidansa na gaskiya,kowa ka kallah awajen Fuska babu Annuri kowa yayi tagumi yana alhinin wannan Rasuwa ta Alhaji Abdulmalik Dankasuwa….

    Itako Malika na Shiga Falon gidan ta tsaya cak tana bin kowa da kallo,gabadaya dangin Daddyn natane yan malumfashi suka cika Falon suna koke kokensu,wanda ada sune in ta gansu sun zo gidansu tayi ta fadan cewa sun zo maula sun cika musu gida,sai gashi yau sune suka zo su taru suyi kukan rashin da kuma Faduwar bango garesu gabadaya.

    Nan idanuwanta suka kai kan Hajiya binta dake zaune gefe da dogon Hijabi ta carbi tana ja,Fuskarta ta kumbura saboda kuka,gefenta kuma Joda ce itama sanye da hijabi tana Sharan kwallah,Shigowar Malika shiya sa Falon ya dau Shuru kowa ya juyo yana kallonta cike da tsausaya domin ansa babu wanda akama mutuwa kamar ita.

    Hajiya ta kalleta idanuwanta da suka sukayi jawur cike da kuka tace”Malika..”Takira sunanta cikin raunin da karayan zuciya,ai da gudu malika tatafi gareta ta Fada jikinta tana Fashewa da kuka,Rumgumeta hajiya tayi itama kukan take tana Fadin”Mun rasa Alhaji malika,mun rasashi lokacin da da ni dake muka fi kowa bukatarshi,wayyo Allah mutuwa tamana yankan kauna ta daukemana Alhaji lokacin da muke tsakar bukatarshi..”Take Fada tana kuka,Malika dake jikinta ta kara fashewa da kuka,cikin muryan kuka wacce ta Dishe take Fadin.

    “Dama da gaske mallam yake Daddylove ya tafi ya barni..? Why..? meyasa zai min haka ? zai tafi ya barni cikin wannan Duniya mai cike da kunci ni kadai,ya rayuwata zata kare,wayyo ni Malika dama Allah ya dauki raina,nima na mutu abinne gawata kusa data Daddyna,domin babu Abunda zan tsinta aduniyar indan na zauna ba ni da kowa sai shi,gashi yanzu Babu shiii..”Tafada tana kara kife kanta akasa tana kuka harda jijjiga.

    Wata wacce take kanwa ga Daddy tataso daga inda take ta riko Malika itama tana hawayen tace”Ashh malika bar Fadin irin wannan kalaman basu dace ba sam,ki na zaton Allah daya bamu shi bai Fimu sonshi bane? karki Manta gawan Mahaifinki na cikin gidanan kuma sai ki sakamai da mganganun banza da koke koke,yanzu ne fa zamu nuna mai mu masoyanshi ne ta hanyar neman masa gafaran Allah,gashi kema baki da lafiya ko so kike kijama kanki mtsala muna alhinin rashin Mahaifinki mukoma alhinin shiganki wani hali..? Girgizamata kai Malika tayi tana toshe bakinta da hannun kada kukanta ya Fito,Zaunar da ita tayi tana zama kusa da ita carbin hannunta ta mika tana Fadin”,Yita salati acikin ranki,Kibar kukan nan hakannan kada kijama kanki wata mtsalan Abdulmalik tashi ta kare ,sai dai mune muke cikin kila wa kalan Yaushe zamu mutu? yau ne gobe ne? bamu sani ba..”Take Fada tana Share kwallah.

    Gabadayan Falon sai da kalamanta yasasu ta kwallah,itako Malika batayi gaddama ta karbin chasbawan tana karanta innalillahi bakinta na motsi ammh hawaye sun gaza daina gudu bisa kuncinta,haka Hajiya binta ma ana ta bata baki,ana mata Fadan tadaina kuka ita da zata Tallafin Raunin malika,ammh itama ta koma tana biye mata suna kukan da bashi da amfani,dole suka hadiye kukansu ammh fa zukata sun Raunana,gabba sun yi rauni suma.

    Tashin hankali bai kara ziyartansu ba sai da akace Hajiya da Malika su fito su zo Falon waje inda aka shirya Daddy,domin sumai addu”a da ganin karshe,lokacin da Malika taci karo da gawan Daddynta kasa control din kanta tayi haka ta fada kanshi ta kamkameshi tana kuka mai taba zuciya kamar zata Shide,hajiya ce kadai ta samu daurewar yimai addu”an Fatan dacewa da kyakyawan mtsayi.

    Malika kin sakin Gawan Daddy tayi Fadi take ita, Daddynta bai mutu kada su Fitar dashi,gashi ta rike makaran dakyau taki saki,sai da Abbi ya fita waje ya kira saleem yazo da karfi gaske ya bambareta jikin makaran yana lallashinta,ammh ita hankalinta ya bar jikinta,ganin tana Fizge fizge ne yasa ya Kara tsaurara rikon dayayi mata,har sukayi baya suna neman Faduwa,neman kwatan kanta take ita sai taje ta riko daddynta kada su Fita dashi,ammh Saleem bai barta ba sai da ya tabbatar da sun Fita da gawan waje kana ya Sausauta rikon nata yana Fadin”Haka mukayi dake..? Haba Malika stop don Allah baki ganin halin da kike ciki ne?”…Yafada yana kallonta cike da tsausayinta.

    Kuri tayimai kafin kawai yaga tayi luu zata Fadi ya tarota yana Salati,ashe suma tayi sai da wadanda ke kusa suka taimako da Ruwa ya Shafamata kana ta Farfado,wannan karon babu kuka da baki sai dai kukan zucci da Fitowar hawaye,kamar an bude fanfo ammh ba mgana,Gashi ta makaleshi gam taki sakinshi,dakyar ta yarda ta koma jikin Joda,ammh sai da ya ce mata zashi jana’iza ne da an kai Daddy gidanshi na gaskiya zai dawo gareta,kana ta sakeshi ya Fice kamar ya mata kwallah.

    Amsallacin jumma’an dake anguwan aka Sallaci Daddy,wanda ya tara dimbin jama”a iya kallanka mallam,agaskiya Daddy ya dace kama daga yadda Annabi ya kwatanta mana Dacen musulmi na kwarai,uwa uba ga Shedan mutane daya samu Abun sai wanda yagani,Amgakabarta ko ba”a matsaka tsinke wasu ma har aka binneshi basu hango ba,saboda tsabar jama”a,Saleem yana daya daga cikin shakikan Daddy wadanda suka sanya kanshi cikin kabari suka turbene da kasa,saboda imanin da Tunanin shima watarana nan za”a kawoshi yan”uwanshi na jini na gani zasu Rufe kanshi da kasa,kai Allah ka Shirya damu kasa mu dace Duniya da lahira.

    Bayan an kaishi gidansa na gaskiya aka dawo ana cigaba da karban gaisuwa bayan an saka Rufunan manya manya cikin haraban gidan da waje saboda mutane,Su Abbi sune gaba gaba wajen karban gaisuwa,Saleem ko yana tare da Sadiq dayazo bayan angama jana”izar Daddy,da wasu yan’uwansu matasa irinsu yan malumfashi,Ba dadewa sai ga su Ummi sun iso,har cikin gida suka shiga inda suka iske malika zaune inda Saleem ya barta tana kwallah ammh ba”a mgana,Ummi ta zauna kusa da ita ta Rumgumota tana ta lallashinta da mata nasiha masu ratsa jiki,hakama Hajiya itama ta dora danata hadda hajiya binta basu kyale ba,suna ta bata baki,don babu shakka mutuwar Alhaji itama ta daketa.

    Sai yammah kana su Ummi suka koma Abuja,haka akacigaba da amsan gaisuwa daga bangarori dadama,ciki harda manajojin gidajen man Alhaji Abdulmalik dankasuwa,tare dana kamfafonimshi,Malika kuwa tunda aka Fita da gawan Daddy bata kara ma kowa mgana ba,sai dai kawai aga hawaye suna zubomata,sallah kadai ke tada ita daga inda take,Abinci ma In Joda ta matsa mata taci sai kawai tarashi ta Shige tiolet ta kulle kanta tana kuka,data gaji da halin data ke ciki ne ta Fita waje taje ta sanar da Saleem,shima Hankalinshi tashe yazo yana magiyan Ta bude,ammh malika taki,yayi yayi,sai ya koma daga ban baki zuwa yimata Fada cikin zafi,ammh kememe Malika taki budewa kuma yanajin kara sesshekan kukanta,wanda ke tafasa mai rai.

    Kada kai kawai yayi ya Fita daga dakin bayan ya Umarci Joda data rabu da ita ta samu natsuwa zata bude da kanta,haka ko akayi sai da tagaji da zaman bayin kana ta Fito tana goge kwallah,ganin ban tsausayi ga cikinta ya girma Tunda ya Shiga watanshi na bakwai kenan,sai daddare kana Malika ta iya shan madaran hollandian da kaza,shima Saleem ne ya ritsata kuma ya matseta ya dinga Turamata abaki,bayan ya gama yakoma aikin lallashi,tana Rumgume ajikinsa,Joda dake kula da Malika in ta gansu awannan yanayin sai ta dinga mamakin yadda aurensu ya kasance,ammh kalli yadda Saleem yake kafa kafa da malika Bayason ya barta tana kuka,Baya barinta sai ya tabbatar da ko bata bar kuka ba toh hankalinta ya kwanta,ta bar koken koken takoma tana ajiyar Zuciya.

    Ranar da”akayi sadakar ukune sai ga Maman Abba ita da megidanta sun zoma Malika da Saleem gaisuwa,Zahrin gaskiya Malika taji dadi sosai haka ta Rumgume Maman Abba tana Fadin”Maman Abba kinga yadda Rayuwata tadawo ko? Babu uwa,uban dani ke kallo amtsayin madubina shima yatafi ya barni..”Take Fada tana kuka,bayanta Maman Abba ta shiga bugawa tana Fadin”Kina da wani Madubin Malika,mijinki shima bangon kine,ina mai tabbatar miki Allah bazai dauke Daddy kuma yahanaki soyayyar Saleem da kulawanshi ba,sai dai ya daukeshi don gwada imaninki,kiyi tawakalli sai kiga Allah ya Dubeki da idon Rahama ya haska rayuwarki,wanda Daddy na cikin kabari Allah zai nuna mishi ke,kuma yayi alfahari dake..”Kalaman Maman Abba ya sanyayama malika rai har sai da ta murmusa tana digan hawaye,sake Rumgume juna sukayi tana kara lallashinsa.

    Joda dake gefe kuwa sai tayi mamaki ganin yadda Malika ta saki jikinta da Maman Abba,wacce ke ta bata baki tare da wasu shawarwari,Itako Malika sai gyada kai take tana nuna alamun gamsuwa,sai yammah sukayi Shirin tafiya,Har waje Malika ta rako Maman Abba tana mata godiya,wanda ganinta haka bakaramin Dadi Saleem yaji ba,kura mata ido yayi yana kallonta,Itako kallo daya tayimai ta kauda kai tana Jin kunya ganin Abokinshi Sadiq na wajen ga sauran Manyan mutane irinsu Abbi.

    Suna sallama da Maman Abba,shiko Saleem shida Sadiq suna musabaha da Baban Abban,ammh kacokan hakalin Saleem naga Malika ganin yadda kawai yaga ta wani rame,kodon bai kara ganinta cikin rana bane,? Sadiq ne ya lura da kallon da yake mata,shima ya kalleta aranshi yana yaba kyanta ba karya,har motar su Maman Abbah ta Fice daga gidan bata koma ciki ba ita da Joda,Ganin haka yasa Sadiq ya zunguri Saleem yana Fadin”Haba Acp wannan dogon kallon ai ya wuce na Shari”a..”?

    Wani banzan kallo ya jefamai kafin ya cigaba da kallon Malika so yake su hada ido ita kuma tana lura dashi sai taki yarda,dariya Sadiq ya Sheke dashi kafin yace”Kuma gaskiya Ba laifi Matar naka akwai kyau,gata jinin Turawa ko banza zakuyita haihuwan Jajayen Fata kyakyawa..”Saleem bai san Dalili ba,kawai yaji mganar Sadiq ta cakanmai rai sosa,wani takaichi ya kumeshi,Kirne Fuska yayi kafin ya fara takawa zuwa kusa da malika wacce ke Shirin juyawa zata koma gida,bai ce mata kala ba,ammh yana biye dasu har suka Shiga Falon gidan,wanda joda ta dingama Malika radan ga Saleem nan na binsu abaya,bata juyo ba,ammh ita kadai tana Sakin mirmishi domin da babu Saleem arayuwarta wannan Rashin ya faru,kila itama da yanzu tana kwance,shiyasa akowani lokaci take jinjina ga gwarzon maza Wato Saleem domin ya zama zakara ne acikin zaratan maza.

    Sai da yaga sun Shige kana ya dawo wajen Sadiq yana kallonshi duka hannunwanshi cikin aljihunsa yake Fadin”,Dazu kace ina kallonta? matarka na kallah ko matata? kuma dakake yaba kyanta uban wa yakai idonka Akan matata? plz mallam wlh karka kara,In so kake ka yaba kyan mace sai kayi aure kaga sai ka yaba naka…”Daga haka yayi Wucewarsa zuwa Rumfar dayake zaune,shiko Sadiq baki ya rike yana Fadin”Au abun harda gori,toh muna kwana nawane inda rai da rabo.

    Washegari sai ga Baban Zahra yazo gaisuwa wato tsohon Alkalin alkalai na kasa gabadaya,Zahirin gaskiya Saleem yaji dadi sosai wanda har cikin gida ya shiga dashi yayi ma hajiya da Malika gaisuwa,bai jima ba ya Tafi,bayan tafiyan ne Sadiq da Abbu suma suka dau hanyar Abuja bayan ya Shiga har ciki an kiramai Hajiya Binta da malika yayi ta musu Nasihan mai ratsa jiki,wanda ta Shigesu,haka suke hawaye kawai don yadda zukata suka raunana babu wani abunda baki ya isa ya Furta,gashi tun yau hudu da rasuwar Daddy mutane duk sun fara watsewa za”a barsu su kadai Abun yazo ya rafkesu.

    Sun tafi ba Dadewa Saleem ya nemi gnin Malika,ganin da Jama”a sosai a baban Falon gidan nasu gashi ita kuma tana sama ne,ita da joda,sai Yan alqawarin nata mery da Dose,Umartan Joda tayi data bude mata wani falo dake ta waje ya shigo,aiko haka akayi Joda ta bude Kofar Falon Saleem ya Shigo sai ga Malika ta Shigo da cikinta gaba,tana sanye da wata doguwar riga mai Tsukakken hannun kamar roba.

    Batama kariso ba ya isa gareta ya riko hannunta suka zauna bisa daya daga cikin kujerin Falon,kura mata ido yayi ita kuma kanta na kasa,ajiyar zuciya ya sauke kafin yace”Ya hakurinmu..? fata dai kinci abinci baki zauna da yunwa ba..? Kai ta gyada mai kafin tace”Hakuri mungode Allah..’Tafada idonta na cikowa da kwallah,Baki ya sake kafin ya dafa duka kafadunta da hanuwanshi biyu yana Fadin”Toh kuma miye Abun kuka? ashe bakijin mgana na,har saunawa zan fadamiki kuka bashine zai dawo da Daddy ba,yatafi kenan sai dai mu tayashi da addu”a Allah yasa chan yafiye masa nan..”Hawayen datake rikewa suka zubomata ta sanya hannu ta share tana Fadin”Na bari insha Allahu..’Tafada cikin wani yanayi.

    Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace”Dama na nemi ganinki ne,saboda ina so na Wuce zamfara yanzu,shine nake so na tambayeki ranar bakwai zaki koma gida,ko kuwa sai kin kara wani satin..? Dagowa tayi tana kallonshi cikin Rauni tace”Yau kuma..? gyada mata kai yayi kafin yace”Eh Tun jiyama naso tafiya,so rashin Tafiyar su Abbi ajin ne shi yadakatar dani,.”Jikinta ne yayi sanyi kwal kwal da ido tana so tayi kwallah,bata fuska yayi kafin ya nunata da yatsa”Karki kuskura hawayen nan su zoba..,Haba don Allah ya kikeso nayi da raina ne,Kullm kuka kullum kuka,Ehe ko kin taba tambayanta yadda kukanki ke kona kin rai ehe..? Yafada yana sakarmata manyan idanuwanshi.

    Rudewa tayi ganin yadda bacin ranshi ya Fito sarari,Kukan take son hana kanta sai kawai ta fada jikinsa da karfi tana tura kanta cikin Faffadan kirjinsa,tana hana kanta kukan dayakeson kwacemata, Riketa yayi saboda tabashi haushi,ammh jin yadda take kara kamkameshi ne yasa ya tabbatar da hakuri take bashi,hannuwansa yasa duka biyun ya Rumgumota yana Sakin ajiyar zuciya yake Fadin”Toh wai miye na kuka daga nace zan Tafi yanzu? kodai baki san na tafi ne..?

    Dagowa tayi ta daga ga mai tana kokarin maida hawayenta,Zuru yayi mata da ido kafin yace”Meyasa baki san na tafi,alhalin kinsan cewa zan koma bakin aiki..”Rau rau takara yi kafin tace”Kabari sai gobe ka tafi don Allah..!Ina son kasancewa tare dakai..”Tafada tana maida kanta jikin kirjinsa Rumgumeta yayi yana sakin wani munafikin mirmishi,Shafa bayanta yake yakasa mgana Lokaci daya ya dago kanta yana kallon kwayan idonta,Kasa juran kallon tayi sai ta hau lumshe ido tana kokarin maida kanta kirjinsa,Bai bata dama ba,sai ma Lebenshi dayakai kan lebenta yana tsotsa cikin wani salo,bata mai gaddama ba,sai ma kara rikeshi datayi tamikamai Harshenta ya kama yana tsotsa cike da kwarewa, kan cinyarsa ya maidata,shikuma ya cigaba da kissing dinta yana Shafa ko’ina ajikinta musassaman cikinta zuwa kasan mararta,Tuni ta Birkicemai lokaci daya itama take maida mai martani tana shafa kanshi zuwa bayanshi hannayenta na kara kaina bisa kirjinsa tana shafa kan Nipples dinshi,Shan yaji Saleem yafarayi saboda jin wani abu na zirgamai,Lafe mata yayi ajiki yana maida Numfashi,hannayeta ya rike cikin wani yanayi yake Fadin”Bari kina tadamin da hankali..”Yafada yana kamkameta cikin wani yanayi.

    Da idonta wadanda ke cike da bukatuwa ta kalleshi,shima ita yake kallo batayi musu ba ta daina tabashi,ammh sai ta kai bakinta saitin Kunnanshi tana Fadin”Am here for u Only mallam..”Tafada tana Shafa keyarshi da hannunta guda daya jin haka yasa ya Birkitota yana kallonta da idanuwansa wadanda suka chanza launi yace”Really….”Yafada cikin wani Shauki kunya ce ta kamata sai ta kauda kai tana kokarin tashi daga jikinsa bai bata dama kawai sai ya mikar da ita tsaye,bai mata mgana ba ya koma ya kulle kofar falon yana dawowa ya Cire riganshi yana kallonta ido cikin ido,kafin ya sanya hannu ya zare mata hijabin jikinta yana binta da kallo,Wuyan doguwar rigar ya sabule mata dama tana babban Wuyane,sai gata tayi kasa zata fadi,da hanzari ta rikota tana kallonshi

    Shishige mata yafarayi yana wani kankance ido,Tokareta yayi da kafarsa hade da kujera yana kama Fuskarta da hannu biyu yashiga bata wani kiss mai zafi yafi minti biyar yana tsotsan bakinta kafin ya Kwantar da ita ahankali bisa kujeran shima yazo ya kwanta akanta,ammh sai yayi gefe saboda cikin jikinta,Tana kallon kwayan idonshi ta dauki hannunshi ta aza bisa boobs dinta,kafin ta rumgumeshi tana Shafa kirjinsa cike da salo da kwarewa,cikin lokaci suka rikita juna bakacin sautin komai sai na tashin Numfashinsu,Saleem yasamu Abunda yakeso,Rumgume yake da ita yana maida Numfashi Dadi da wahala lokaci daya..

    Saboda jaraba irinta Saleem da samun waje kakumarta yasake yi,Yakara second round,domin kwata kwata baya gajiya da tsaga jikin malika tana da wani sirri dake rikitashi sosai wanda ko yanzu yagama Having Sex da ita,toh sha’awarta zata dawo mai sabuwa,sai gashi tare sukayi wanka a bedroom din dake dakin dama akwai bedroom Saleem ne yake ra”ayin yau din Asaman kujeran za”a kashe arnan😂🙈suna gamawa Ya je mota ya Dauko kayanshi ya sauya kafin yakoma ciki yayi ma su Hajiya sallam,kunga Malika yadda ta makaleshi gabansu Hajiya da Joda da yan Malumfashi tana kuka Wurjajan,Wai bazai tafi ba,shi yau yaga ikon Allah,Dakyar da Sodin goshi ya lallasheta ta sakeshi shima sai da yayi mata alqawarin Ranar bakwai zai zo ya ganta,duk da haka bata ga tafiyarshi ba daki ta koma tana kuka,shikanshi jikinsa ba Dadi ya tafi bai san dalili ba yanaji kamar Malika ta dauwama dashi har karshen rayuwarsa ba,bai yi Kukan rashi da kewarta ba sai da ya koma gida yayi kwance kan gado yana Tunaninta,Zahra ko tana ta nacin kira yaki daga kiranta saboda in yana cikin halin Kewa da Tunanin malika baya bama komai muhallin hanashi ko dakatar dashi.

    _______________________

    *BAYAN KWANA BAKWAI..*.

    Ranar addu”an bakwai da Wuri Saleem yazo,shima Abbi yazo shida Ummi ammh basu jima ba suka tafi,shima saleem bayan gama addu”ar yace joda ta kiramai Malika shi zai koma,Kin fitowa tayi tana chan saman dakinta tana kuka,dole tasa Saleem ya Shiga har saman da kanshi yadda ya ganta Abun bai mai dadi ba duk takara ramewa akan yarda ya barta Ranshi ya baci ya fara mata Fadanshi da bataso,Ai sai ta Rude ta sauko daga kan gado tana bashi hakuri ammh yayi banza da ita ta inda yake Shiga batanan yake Fita ba,daga karshe yace indai tana mai Taurin kai Allah bazasu shirya ba.

    Hanyar Fita yakama da hanzari ta mike ta isa ta bayanshi ta Rumgumoshi tana kuka take Fadin”Don’t leave me..Don’t..”Take Fada tana kuka cak ya tsaya yana jin kukanta na ratsa ranshi,Juyo wa yayi yana Riketa da wani karfi ta fada jikinsa ta kamkameshi tana kuka,Shima maida hannuwanshi bayanta yayi yana sakin ajiyar Zuciya,Shafa bayanta yake zuwa kasa Tudun hip dinta cikin wani salon lallashi yake Fadin”Fisabillahi Yanzu Abunda kikeyi daidai ne? Sau nawa zan fadamiki Kidaina wannan koke koken,? Kokuwa dai wulakanci da kuma raini ne ke damunki Tunda nace bani son kukanki wato in mutuwa zanyi na mutu ko..?”Da sauri ta dago kanta tana girgixamai tana hawaye,hannu ya sanya ya Sharemata hawaye yana fadin”I already tell u no more kuka indai ina tare dake,to meyasa kike yi koda yaushe.?.”Tana rike hannunshi tana kara share kwallah tace”Nabari..Nadaina wlh..”Tafada cikin sanyin murya,Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya Rumgumota jikinsa yana kamkameta Idanuwansa suna Rufe yaji ta Furta”I miss u…”Shikanshi Shaukin kewarta ne yasa ya Furta mata”Me tooo…”Cikin muryan So da muradi.

    Bai mata komai ba ranar ammh kafin yatafi sai da yalugwigwitata son ranshi,Kuma yayi mata wanka ya bata abinci kafin ya tafi ya barta wajen Hajiya da joda zuwa wani satin yazo ya tafi da ita,bai bari tasan tafiyarshi ba daga Fita salla ne bai dawo ba,sai dai ya kirata awaya yace yatafi,saboda yasan sai tayi kuka,shikuma kukan tane sam bayaso,Akwai sunsha kuka ranar ita da hajiya barima da duka jama’ar Malumfashi duk suka koma aranar ko mazan dake waje ba kowa,Tuni kowa ya watse,wadanda suka tsaya shakikan Alhajin ne Na Malumfashi,ranar mutuwar ta dawo musu sabuwa gida yayi rakwa rakwa,ranar Malika da zazzabi ta kwana saboda kuka,da Joda ta mtsamata tasha panadol taki sai tace mata zata kira Saleem ai da hanzari tatashi da karba tasha takoma ta kwanta tana maida numfashi lokaci daya da hawaye,itako Joda sai da murmusa tana yaba tsarin wannan Soyayyar mai cike basarwa domin duk wanda ya kalli malika yasan Tana cikin mayen son mijinta,haka shima soyayyar Malika bata boyiwa acikin idanuwansa ba,sai dai shine yake kokarin boyeta da karyata kanshi da wai amanace gareshi gata marainiya ba Uwa ba uba.

    Haka suka ciga da zama ita da hajiya da joda Da su merry wanda zuwa kwana goma kowa ya watse sai wata goggo talatu kanwa take ga Hajiya suma zaune tare,Tun zuciyoyi na kuka suna bayyana digan hawaye har suka gaji suka dau dangana suka koma kukan zucci,Ranar da Daddy ya cika kwana 14 da rasuwar tun Safe Malika tayi Shirin komawa ita da Joda wanda Hajiya tace su tafi tare ta rinka taimakamata da wani abu saboda yanayin Jikin na malika,aiko taji dadi sosai,Saleem ya kirata yace Direba yakawo ta shi bazai samu zuwa Meeting suke dashi..

    Da zata tafi haka ta kamkame hajiya ta kuka dakyar aka bambareta daga jikin hajiya,wacce itama kukan mutuwar ta dawo mata sabuwa,mota kawai Malika ta Shige tana kuka mai ban tsausayi dayake dama already sun Saka duka akwatun nan kayansu cikin booth din motar wanda Direba zai kaisu,cikin daya daga cikin motocin malika ne sanda tana ganiyarta.

    Sai da suka iso gida kana Malika ta kira Saleem ta fada mishi isowarsu,azahirin gaskiya ya nuna murnan sosai,har saida sautin mirmishinsa ya Fito Fili,joda ko gyaran gidan tafara harda kichen sai da ta share ta goge datayi mganar girki ne malika tace tabari Mallam ya dawo don ita tunda tazo bata taba girki ba,Tunda bama iyawa tayi ba.

    Sun idar da sallar mangariba kenan sukaji hon din Shi megadi ya wangalemai get ya Shigo,jikin malika na rawa ta mike daga kan Darduma datake tana sakin Mirmishin jin dadi ga cikimta wanda yayi girma cikin doguwar rigar Material dake jikinta,da kallo joda ta bita,tana mamakin babu Abunda ke sanya Malika mirmishi sai Saleem Tun bayan rasuwar nan shine ganinshi ke sanyata mirmishi,kuma tafiyarshi ta sanyata kuka

    Joda bata gama mamaki ba,sai gashi yayi sallama bayan ya sawo kanshi cikin daki yana sanye da Uniform dinsa Harda hulanshi hannayenshi rike da manyan lodojin reasaurant har guda bayu,da malika yaci karo tana tsaye tana kallonshi cike da kewa,cogewa yayi yana binta da kallon Sha”awa baisan dalili ba,duk sanda yaga malika sai yaji yafi kowani Namiji sa’an mace mai kyau da tsarin jiki na mata.

    Yadda ya saki baki ne yana kallonta yabama Joda dariya,wanda tana ma gaisheshi bai ji ba,yana chan ya saki baki yana bin Malika da kallon sha”awa bata gama dariyan ba taga ya ijiye lodojin hannunshi asaman cafet din daki ya ware ma Malika hannu yana Fadin”Oya *YAR AMANATA..* Come here…’Yake fada yana sakin mata wani kayatattacen mirmishi.

    Itako kunya duk sai ya kamata ganin Joda tsaye,ganin taki zuwa ne yasa ya isa gareta da sassarfa ya Rumgumeta kam yana Fadin”Idanuwanki suna cike da kewata,ammh kinki ki Nunamin yadda kikayi kewata ko? Yafada yana tusa kanshi jikin Wuyanta

    Da hanzari joda ta bude kofa ta Fice tana yar dariya ita kadai.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!