Maleeka Malik – Chapter Sixteen
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
Tun tana saran Fitowarshi har taga bashi da niyyar Fitowa,sai chan sai gashi ya Fito,sanye da wani Towel mai dan girma,hannunsa kuma yana saman kanshi dauke da wani karamin Towel din yana goge ruwan dake kanshi
Kallo Daya tayimai tayi Saurin Sadda kanta kasa,saboda yadda ya Fito gabadaya kirjinsa dake lullube da gargasa,awaje yana maiko Ruwa yana bayyane,Suffar karfin hannayensa ma”ana muscles suma sun bayyana waje,shima ko barayinta bai kalla ba,balle ya tankata ko yasan akwai tsayuwar mutum awajen.
Wajen Dressing morrior dinsa ya nufa,yafara Shafe jikinsa da lotsin dinsa mai dadin kamshi,har yagama yayi cumbing din sumar kanshi bata ko kara motsi daga wajen ba,Wucewa yazo yi ta gabanta zai isa wajen wardrope dinsa,kafarta dake wajen ya bangaza kamar bai gani ba,nan ko da gangan na haushi ya hadamata Ruwan wanka ne.
Jaye kafarta tayi tana Kwabe Fuska saboda taji zafi ko kallonta bai yi ba,yakarisa wajen wardrope dinshi ya bude yana dauko kayan da zai saka,wasu riga da wando ya dauko Blank and white ne,ada yaso sanya kayan agabanta sai wata zuciya tace”Saleem in har ka bari yarinyar nant taga girmanka toh daga yau shikenan ta gama rainaka gwara ka Rufama kanka asiri kaja girmanka..”Jin hakane yasa ya kwashi kayanshi ya Shige tiolet yana wata waka na ” _Babe i love u,…Babe i kiss u..Babe i need u…._”
Da kallon mamaki ta bisa tana gimtse baki,bai dade ba ya Fito daidai sanda Ummi tayi Knoking din kofar kafin ta turo,Da Malika taci karo zaune inda ta barta,cike da mamaki take kallon Saleem dake tsaye yana faman gyara Botiran gaban riganshi,Ganin tana mai wani kallo ne, yasa ya gimtse Fuska yana Fadin”Ummi menene naga kina hararata,ko haryanzu baki bar jin haushina bane..?
Dakuwa ta sakamar tana Fadin”Kaniyarki da Ummi,don mai garinku kumo ina Abunda na sakaka..”?Tura baki yayi kamar yaro yana Fadin”Toh Ummi don Allah bayan na hadamata ruwan wanka so take najata bayin nayi mata? itace inaga bata ra”ayin wankan..”Yafada yana zakuda kafada.
Haushi yakama Ummi ta kalli malika tana Fadin”Diyata ya baki tashi kinyi wankan ba..”?Kwalkwal malika tayi da ido zatayi mgana suka hada ido da Saleem yako zabgamata harara yana kada mata harshe ganin haka yasa Ummi ta kaimai Duka akeya tana Fadin”Fice kaban waje Maketacin miji kawai..”Dafe kansa yayi yana kallon Ummi kamar zaiyi kuka kafin yace”Kai Ummi,yanzu ni ace kamata ban girmi da fada da duka ba? kuma ma wai agaban wannan yarinyar,plz Ummi don Allah kidaina min Fada agabanta sai kisa ta rainani aie..”Yafada yana hade rai kyace wani ubanta.
Tsaki Ummi taja tana Fadin”Shin zaka ficemin ne,ko kuwa sai na nuna maka kalata yanzu nan..? Juyawa yayi yana Fadin”Meye Zafi lauyan Abbi,Allah baki hakuri Ummin Saleem da marwan,da munafukar nan Saleema..”Dariya ta kama Ummi ammh sai danneta har yafice ya Rufo musu kofa.
Maida kallonta tayi ga Malika tana Fadin”Meyasa baki shiga kinyi wankan ba dota..”? Dukar dakai tayi kafin tace asanyaye”Ai bansan ya hada bane,bai Fadamin ba Ummi..”Mirmishi Ummi ta mata tana Shafa kanta tace”Ok tom Shikenan barni dashi,yanzu tashi maza ki Shiga kiyi wanka kizo kiyi sallah kinji ko..? Kai ta gyada mata tana mikewa,Hannunta Ummi takama har kofar bedroom din tana Fadin”Ki saki jikin ki kinji ko? nan zan kawo miki abincin naki,ko zaki Fita Dining tare damu..? girgiza kai tayi kafin tace”Bazan iya cin komai ba Ummi..
Kallonta tayi kafin tace”Meyasa.. ?Kanta na kasa tace”Ina son naci buh ammh ko naci Sai nayi amai..”Takarishe Fada hawaye na cikomata ido,Dafo kafadunta Ummi tayi cike da tsausaya tana Fadin”Ayy srry,sannu kinji haka kowacce uwa tagari ke Fuskartan,ki daure ki dinga ci ko yayane, saboda abunda ke cikin ki,kuma koda kinyi aman ko ba duka ba,wani zai tsaya kinji..? Gyada kai tayi hawayen nata na zubowa cikin so da kauna da tsausayinta ta sanya hannu ta sharemata kafin ta bude kofar bedroom din tana Fadin
“Yi maza kiyi wankan ki Fito,kan kigama sallolinki na kawo miki Abinci..”Batayi gaddama ba ta Shigen makeken Tiolet din mai kama da Falo guda,bin ko”ina da kallo take tana jinjna tsarin bayin,ammh wannan ko rabi da kwatan tsaruwa da haduwan nata bai kai ba,wasu kwallah ne suka zubomata tasa hannu ta share,ko acikin bath din kuka tayi tayi kafin ma tayi wanka tana Tuna sanda tana Gida komai sai dai ayi mata,ammh ga yadda rayuwa ta maidata.
Sai da tagama wankan kana ta dauro alwala ta Fito,daure da tawul,akwatunta ta bude ta ciro kayan shafanta ta shafa kafin ta nemi wata doguwar rigarta Red colour,ta sanya wanda take da budadden hannh,tana tufke gashin kanta ne Ummi ta Shigo dauke da kololi abinci bisa wani katon Tire mai girma,Tana ganinta ta washe baki tana Fadin”Yauwa kefa,kinyi sallah ne..?
Girgiza mata kai tayi tana dukar dakai,Gefe Ummi ta ijiye mata katon Farantin bisa cafet din dakin tana Fadin”,Toh maza kiyi kizo kici abinci kada ki zauna da yunwa kinji ko.? Gyada kai tayi kafin tace”Tanque Ummi..”Mirmishi Ummi ta mata kafin tace”don’t kinji..Is my Duty…”Daga haka ta Fice daga dakin.
Ajiyar zuciya ta sauke aranta tana Fadin”Zuciyar iyayansa mai kyau,ammh shi ko ina ya gado bakin hali oho..”Bata gama mamaki ba ya sawo kai dakin waya makale akunnenshi yana waya,bai kalli inda take ba,illah Fadawa dayayi bisa makeken gadonsa yayi Ringigine,yana cigaba da amsa wayarsa,da ga duk alamun yadda yake mganar zaka san wanda yake wayarshi dashi bayi da wani muhimmanci saboda yadda yake bada amsa ayangance daga baya ma tana ji ya yanke kiran yana sakin wani Siririn tsaki.
Tsayawa tayi kyam tana kallonshi daga saman Fuskarshi zuwa kirjinsa,yadda ya Lumshe idanuwansa kamar mai barci bayan ya goya duka hannuwansa bisa kirjinsa,ta Zurfafa da kallonshi tana yaba kyau da tsarin Fuskarsa bata ankara ba taga ya bude idanuwansa ahankali yana kallonta,Daburcewa tayi tana Zare ido kamar wacce tayi karya Bai mata mgana ba,illah juyamata baya dayayi yana Sauko da kafarsa daya bisa cafet din dake dakin,ganin haka yasa ta jingina da wardrope din dakin tana sauke wasu tawagen Numfashi,Ta hanzari ta dauki hijabin data cire,ta saka bata san gabas kawai ta tari yammah ta tada sallar tana ta buga Shirmen data saba.
Kamar ance ya waiwayo,sai yayi mugun gani,Ware ido yayi yana kallonta tana sallah,na farko ba gabas take kallo ba,na biyu wlh bakinta baya motsi baijin tana karantana wani Abu,daga sujjadan har ruku”un yi kawai take kamar wacce take dukawa tana duba wani abu,bai gama mamaki ba yaga ta zauna tahiya tayi Shuru kawai ta kurama waje daya sai chan kuma ta sallame,kara mikewa tayi zata kabbarta wata sallan da hanzari ya diro daga kan gadon sai gashi gabanta da kakkausan murya yace”Ke tsaya da sallar nan naki don Allah…”
Yafada yana tsareta da ido,ba alamar wasa,jagale tayi atsaye tana raba ido,Habansa yakama da hannu yana Fadin”Ke yanzu sallar me kikayi..? Kanta na kasa tace”Na Azahar.. Jinjina kai yayi kafin yace”Ammh dai baki karanta Fatiha da sura ko? don naga ko minti daya bakiyi kike dukawa..? Dagowa tayi tana kallonshi ganin yadda ya tsareta da ido ne yasa ta sadda kai cikin sanyin murya tace”Fatiha kadai nake karantawa..”
Dan ware ido yayi kafin yace”Why..?ko bakisan raka,”a biyun Farko Fatiha da sura bace,sai a raka’a biyun karshe ne zaki karanta Fatiha kadai..”Jim tayi kafin tace”Menene Sura,Ai ni d only Fatihan na iya..”Baisan sadda ya sauke ahannunsa ahaba ba yana binta da kallon mamakin kin Wuce Tunanina,jin shuru yasa ta dago tana kallonshi ganin yadda yake kallonta kamar na rashin hayayyaci yasa taji jikinta yayi sanyi sosai,nan da nan idanuwanta suka cika da kwallah.
Bai samu zarafin mata mgana ba, saboda mamakin dayakeyi kai tsaye yasake jefomata tambaya”Guda nawa ne Farillan alwala,kuma nawa ne Sunnoninsa..? Bata dago ba,taji hawaye sun taho mata bata taba nadamar rashin ilimin addinin ba irin na yau,in da ta iya data ba Saleem amsa koda ta muzantashi kamar yadda yayi mata,sai dai kash bata san komai ba.
Ganin tayi Shuru yasa ya bude baki yace”,Shima baki sani ba ko..?Kai ta gyada mai ahankali tana kokarin maida kwallar data kusa zubomata,baki ya rike yana binta da kallon Ina da aiki,kai tsaye ya sake cemata”Ke wai tsayama,Kina wanka inda Janaba ta sameki,ko kuwa kina tsarkake kanki inda kin gama jinin al”ada..? Yafada yana kara saka mata ido kur yana kallonta.
Tsuru Tsuru tayi da ido tana kallonshi kafin ta sadda kai kasa tana wasa da gefen hijabinta,Miyan bakinshi ne yaji ya kafe,saboda yadda yaga yanayinta bama sani tayi ba,mikewa tsaye yayi yana goya hannunshi abaya yace”Tambayarki nake ki sanar dani in baki sani ba,kada ki cucu kanki..? Kanta na kasa tace asanyaye”Eh ni bana kowani wanka,sai wankan da kowa yakeyi kamar wanda kayi yanzu ko bashi ba..? Ware ido yayi kafin yace”Na bani ni jikan Hafsat…Kina nufin kice ko Jini kika gama baki wankan tsarki? balle ma na saran ranar dana kusance ki bayan kin dawo hayyacinki kin Tuna dayin wankan Janaban? Yafada idanuwansa sun Chanza launi.
Kasa kawai tayi da kafafunta tana dukawa kanta na kasa ta Furta..”Wlh bansa komai ba,ban iya bane danayi,…”Tafada hawaye na zubar mata kamar an bude Famfo,kugu yakama yana kallonta,kawai sai wani shashe na zuciyarsa yatsausayamata matuka na yadda tana yar musulma ammh bata da sani kan Addininta.
Ajiyar zuciya ya sauke yana Fadin”Is ok..Kina so na koya miki Karatun Addini..? da hanzari ta gyada kai tana Fadin”Eh plz…”,Bai mata mgana ba illah Mikamata hannu dayayi yana kallonta,itama kallonsa take kafin jiknta asanyaye ta saka hannunta bisa nashi ya mikar da ita,yana jaye da ita har cikin tiolet din bai Direta ko”ina ba sai bakin Sink yana Fadin”Sake alwalan ki nagani..?
Batayi gaddama ba ta duka ta sakeyi yadda ta iya,Girgiza kai kawai yake domin ita kanta alwalan bata iyata ba,haukanta kawai take,Baya yayi da ita kafin ya fara nadadde hannun Rigansa yana Fadin”Juz wacth me verg well kinji..”Gyada kai tayi tana kallonshi yana alwala,sai da yamayamata sau uku kana ta sake yi sau Daya,normal kamar yadda yayi mirmishi yayi mata yana Fadin”Tafiyanmu zata daidaita matukar kina da saurin Fahimta.
Haka suka koma Dakin,da zuciya daya yake koyamata sallah yana mata bayanin komai daki daki,bai samu damar koyamata wani abu ba,sai da yasata ta rama duka salollinta,Isha”i ne kadai yaja musu jam”i bayan sun idar ne ya kalleta yana Fadin”First abunda zamu fara,shine gyara sallanki,yanzu gobe zan saka asiyo miki Karamin Qur”ani izifi biyu,Da Sauran kananun littafin da zasu taimaka miki,yadda zaki fara gane komai daki daki,ammh yanzu kici abinci kizo na fara koyar dake Abun ake Fada yayin Sujjuda,da kuma yayin Ruku”u zaman tahiyan farko da zaman tahiyan sallama..”Gyada kai cike da gamsuwa sai ta samu kanta da furtamai”Tanque…”,
Bai kalleta ba yace”No godema Allah..”Kallonsa tayi araunane batace komai ba,tashi tayi ta isa ga farantin da Ummi ta kawo mata,Kolan Farko ta bude ta iske White rice,sai kula ta biyu kuma Miya ne wacce taji kazi,kadan ta diba ta Rufe sauran,taji dadin abinci sai da cinye wanda ta diba duka harda kari,tasha Ruwa,yau anci sa”a batayi ammh ba,nan ta bar komai awajen,ammh takasa tashi,tana Tunanin kamar bai kamata tabar komai awajen ba,sai ta tuna tana gida Hajiya ke daukemata ko Su Dose da merry,.
Satan kallonshi tayi sai taga baya tatata,domin hankalinsa na kan wayarshi yana Faman latse latse,sai lokacin Ta tuna da nata wayar,batama kunnata ba sai gobe,ganin yadda tayi Tsuru awaje dayane yasa yace”Kinga malama in zaki so na koyar dake kizo,in muka kina ganin zai zama takura zan kwanta ne..”,Jin haka yasa ta mike da hanzari ta isa gabanashi tana Fadin’,Gani ina so plz..”
Tashi yayi daga kishingiden dayake akasa yana tankwashe kafa,tun kafin yayi mata mgana ta tankwashe kafafunta itama,kallonta yayi yana nazarinta kafin yace”Kina bukatar Abun Rubutu,ko hakan daliban ilimi ke zuwa..”Wiki wiki tayi kafin ma tayi mgana ya tashi ya dauko mata wani karamin joter da Pen,shikuma ya bude Dirowan gadonshi ya dauko karamin Qur’aninsa izihu Sittin ya bude yana Fadin”Fara karantamin Fatiha tukunnah naji..”
Gyara zama tayi tafara karantamai yadda ta iya,Sai da tagama kana shi ya sake biyamata cikin Taushin murya da kira”a mai dadi,yayi mata gyaran sosai acikin nata karatun,sai da yayita maimatamata kafin yafara karantamata tana amsawa,bai kyaleta ba sai da Fatihan ta zauna bisa kanta sosai,kafin ya karbi Joter din daya bata ya Rubuta mata abunda zata Fada yayinda Sujjuda da Ruku”u da yayin Zaman tahiyan farko data karshe,wato Tahiya da salatin Annabi ya mika mata yana Fadin”Ki rike wannan,kidinga bita har ya zauna miki,zuwa gobe zan fara biya miki kananun Surorin kinji ko..?…
Karba tayi bakinta na motsi bai bari tayi mgana ba,ya mike yana shafa kanshi ya Fada tiolet,Itakuma sai ta samu kanta da bin bayanshi da Kallo kafin ta Furta ahankali”He is so nice…”,Tafada kafin ta mike tana Fadin”Alhamdulillah na samu *MALLAM*…”Ta fada tana jin dadin Abun har ranta,Jotern tayi ta dubawa tana zaune gefen gado,dayake yayimata Rubutun cikin kalmomin hausa,ammh kuma da Turanci yadda zata gane sosai.
Har yafito tana zaune awajen alwala ya dauro yazo ya Shimfida darduma ya fara shafa’i da Wuturi,tun tana bin karatun har tafara hamma,saboda gajiya batasn sadda ta sulale bisa gefen gadon tana barci ba,shine daya idar da sallahn yazo ya gyaramata kwanciyar ya rufamata blanket,Shikuma bisa sallanyan ya yada Filo ya kwanta bayan ya Tube rigansa dagashi sai dogon wando don baya Hunce gaban yarinya ba ta rainashi,joter nata ya adana mata saman Side drower din gadon,addu”a barci yayi ya kwanta bayan yayi kasa da Hasken dakin ya kunna Dumlight.
*WASHE GARI*
Yau Saleem bai samu Fita masallaci sallar asuba ba,saboda malika,bayan ya jasu sallar sun idar yayi musu addu”o’i sai ya dauko Qur”aninsa ya biya mata Sura daya,Suratul Nas,yayi ta nanata mata harya zauna mata,sai kuma ya koma kara nanata mata Abunda ya Rubuta mata jiya,shima sai da ya tabbata ta iya wasu,babu laifi ya lura kwakwalwarta naja,tana da sharp brain sosai yarinya,ya yabamata ta wannan bangaren.
Basu tashi daga karatunta ba sai da ya sanar dani yadda addini ya koyar damu mu”amala da mutane,ya sanar da ita babu kyau yima wanda ya girmeka rashin kunya ko mgana gatsal,kana ta koyi mu”amala da mutane da kuma girmama Manya,kuma yana daga cikin al”adun mu na hausa Fulani taimakon manyanmu,da koda munga suna wani aiki,yana daga cikin tarbiya sakaya sunan wanda ya girmeka ko ya kusa haihuwanka koda bai haifeka ba din,Kuma ya sanar da ita babu kyau girman kai,ko izigilanci duka haramun ne,zalunci Allah yahana kanshi kuma muma bayinshi yahanemu da yinshi,daga karshe ya sanar da ita Tayi Istigifari ga laifinta na baya Allah gafirun rahimun ne.
Jinjina kai kawai takeyi tana jin dadin mganarshi,balle yadda yake mata mgana cike da dattako ne da kuma jarumta babu alamun sanayyah kawai yana koyamatane don taimakonta,daganan yace su dakata da karatun sai anjuma da daddare zai dora mata daga Abubuwan da suke wajabta wanka,da kuma shi kanshi wankan..”
Yana kokarin tashi ne ta katseshi ta hanyar cemai ” *MALLAM..* Ina da tambaya…? Yajita sarai ammh sai ya barsa wayarsa ya laluba yana kallon lokaci kafin ya waiwayo yana Fadin”Ba sunana Mallam ba,kirani da Saleem dina kai tsaye..”Mirmishi ta sakarmai mai taba zuciya wanda sai da ya tsaya yana kallonta.
Motsa bakinta tayi tana Fadin”Nasani ba sunanka Mallam buh awajen malika kai Malamina ne,wanda yake kokarin tsamoni daga duhu zuwa haske,Ina da mahaifina ammh bai tsaya ya koyar dani yadda zan samu aljannata ba,duk da ban tashi hannun duka iyayena ba,ammh duk da haka bazan ki jinjinama Daddyna ba,domin shi yayi kokarin min gata wajen Tilastani aurenka,Bansan da wani baki zan godemaka ba mallam buh komai miye ina maka fatan Allah ya baka mai saka maka Fiye da yadda kamin..”Tafada hawaye na gangaro mata.
Jikinsa ne yayi sanyi sai yayi saurin komawa ya zauna gabanta yana Fadin”Kin yarda ni malamin ki ne,wanda zai koyar dake hanyar tsira..? gyada mai kai tayi tana sharbe hawaye.,Daure fuska yayi kafin yace”To yazama dole duk Abunda nace kiyi do it ba gardama,? ta gyada kai kawai alamar gamsuwa,jinjina kai yayi kafin yace”Kizama daliba mai biyayyah da niyyar Neman ilimi,kuma mai biyayyah akowani lokaci,sai kiga Allah yabaki nasara kan Abunda kike nema..”
Gyada kai tayi tana Fadin”Insha Allahu mallam,ngd sosai god bless u…”Cije baki yayi yana Fadin”Yi tambayarki,barci ne a idona..? Dukar dakai tayi tana Fadin”Dama game da abubuwan dana aikata abayane,shine nake tambaya,duk Allah zai iya yafemin..? Mikewa yayj tsaye yana gyara zaman jallabiyan jikinsa yake Fadin”Mezai hana,kin manta karatuntunmu,abaya na sanar dake Allah gafirull rahimu ne,so kiyi tuba zuwa garesa tare da Alqawarin da kuma yakinin bazaki koma ga zunubin ki na baya ba,ki kuma yawaita istigafari,Allah shi kuma zai Yafe miki..”Yana gama fadin haka ya haye gado yana lumshe ido,don har ga Allah bayanshi ya gaji da zama.
Itako nan ta zauna tana bitan karatun daya koyamata,sai da tagaji don kanta ta hakuri itama nan bisa sallanyan barci ya kwasheta,bata Farka ba sai da taji Ummi na tashinta,kuma lokacin wani zazzabi mai zafi yagama Rufeta ko iya bude ido batayi saboda zafin jiki,goshinta Ummi ta dafa tana salallami,fita tayi taje ta sanar ma Abbi,shikuma ya kira Saleem wanda already ya dade da Fita
Malika dai ranar haka ta Wuni da zazzabi,Hajiya babba ne tace ita irin cikinta kenan zazzabi da kuma amai domin wunin ranar hararwa tayi tayi kome taci sai ya Fito,dole ta hakura da cin komai,sai da yammah ne Ummi ta mata tuwo miyar kubewa,sai gashi ko taci sosai kuma batayi aman ba,Wuni Ummi tayi ita da Hajiya suna dawainiya da ita,haka Abbi bini bini ya leko yana tambayan ya jikinta,ita dai taga gata a Duniya,sai da wajen yammah ne taji zazzabin ya barta ta Rarrafa tayi wanka,ta sauya kaya tayi sallar mangariba,Sai lokaci Saleem ya dawo daga cikin gari,kuma bai manta ba ya taho mata da Abunda yayi mata alqawari,Qur’ani izu biyu,sai Ahalari,sai Bagadadi,sai bari wa biba,da littafin koyan baki,dana koyan Rubutu duk ya siyo mata,ammh ranar basu samu damar karatu ba,don Tunda takara cin tuwon da Ummi tayi mata tayi ta kelaya Amai,sai kuma zazzabi Daga baya,duk rashin imanin Saleem sai da ya tsausayama malika ganin yadda take bari da jiki saboda zazzabi,sai gashi saboda halin datake ciki bai iya kwana akasan ba,sai bisa gadon ya kwana kusa da ita yana kula da ita,duk da basu hade da juna ba,kowa na gefe,sai dai in yaji tana hada hakora sai ya waiga ya mata sannu,ya maida kai kawai aransa yana ayyana jibi jibin zai koma bakin aiki bazai iya da wahala ba.
Ammh sai me washegari Sai Malika tatashi garas kamar ba ita,sai kuma Aranar ne ta kunna wayarta ta kira Daddyta da hajiya suka gaisa sun dade suna mgana dashi yana ta kara bata hakuri da Umartanta datayi biyayah ga mijinta,ada taso ta sanar dashi tafara zama cikakkiyar mace mai daraja,sai kuma ta fasa ta Fiso ta bashi mamaki ne,har tabama su Ummi waya suka gaisa da hajiya binta cike da fara”a.
Tunda taga ta Samu sauki sai ta dukufa kan duba bitan karatunta Tunda dazu da safe ya bata qur”anin daya siyomata hade da sauran littafan,yanzu surorin dayayi mata take so haddacesu,mganar sallan ta kuwa tuni babu abunda bata gane ba yanzu sai dan Abunda ba”a rasa ba.
Zaman shuru ne yayi mata yawa adakin ta tattaro littafanta tafito Filo ta zauna sanye take da riga da wando na pakistan red and black,sai wani red vail data yane kanta dashi gefenta hajiya ce wacce ke zaune tana kallon Tibin dake ta dimi shi kadai,ammh ba fahimta take ba,wani lokacin in malika bata gane wani waje ba, ita take nunawa ta gyaramata ko ta tadata,Hakika Su Ummi sunji dadi domin ko bakomai ilimantar Da mace ma lada ne,balle kuma Abu ne mai kyau miji yadinga karantar da matarshi domin sunnar ma”aiki ne hakan.
Ta dukufa abitar karatunta taji sallama daga saman kanta tana dago kanta suka hada Four eyes da mai kama da Saleem,sak sai dai ita tafishi manyan ido,da Dan kiba kadan, dauke da wata katuwar jaka,irin ta baya din nan,sai katon trolly dinta wanda take jaye dashi,kallon kallon sukama juna kafin saleema ta dauke kai tana yatsina fuska,wajen hajiya ta nufa ta fada jikinta tana fadin”Oyoyo hajiyata i miss u…”
MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
