Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
    “”Sati Hudu cur Malika ta kwashe a general hospital tana samun kulawa kafin ta warke sumul abata sallama,shiko Alhaji Abdulmalik sai da yakara sati daya akan na Malika kafin shima sallameshi su rankaya su koma gida.

    Ba laifin an samu cigaba sosai game da laluranshi,domin sun dorashi kan mgunguna,ga kuma gashin kashin dasukeyimai kullum,shiya taimaka wajen fara motsi da hannushi zuwa kafadanshi,shiyasa suka sakasu suka siya wata wheelChair,wacce daga kasar China ma,akayi odarta,wanda take hade da rimot din sarrafata jikin keken,basai an Tura mutum ba,tana da Abun control dinta ajiki,duk inda mutum yake so yana daga zaune sai ya danna ta kaishi ko”ina yakeso indai acikin gida ne.

    Koda kafin Asallameshi ya dawo gida Tun yana asibitin Hajiya binta tayi tayi dashi ya bari su Fita dashi waje,ammh Alhaji Abdulmalik yaki bari afita dashi zuwa kasar ketare domin nema mai mgani,yace ta kyaleshi kila haka Allah keson ganinshi,ta kyaleshi kawai baya bukatar aje dashi ko”ina,hadda yan”uwansa ta hadashi,ammh yaki yarda da zencensu Dole suka rabu dashi basu da yarda zasuyi Tunda yaki yarda.

    Jinyar Nashi sai takoma gida,wajen Hajiya Binta,duk da koda yana asibitin ita keda alhakin kula dashi,duk da kawu Shitu na taimakamata,toh yanzu ya koma gida,saboda hidimar gabansa da kuma iyalansa,joda ce kuma ta koma mkranta duk da yanzu wahalar ta ragu Malika ta warke sai Abunda Ba”a rasa ba na damuwa.

    Yanzu Malika takoma kamar ba itaba,mgana ma sai yazama dole takeyi,kosu Dose da mery sunga chanji,don yanzu suna gama hadamata Ruwan wanka zata sallemesu,ta shiga tayi da kanta,ita yanzu kunyarma Duniya ta isheta,domin tariga data sani cewa lbrinta,da mummunar gaddararar daya sameta yagama zaga Duniya,shiyasa ko Excorts dinta duk ta sallamesu,Joy da peter kadai ta bari sai su mery da Dose,suma saboda masu kula da hidimarta na yau da kullum ne.

    Gidan ko Da Alhaji Abdulmalik ya mallakama Saleem ko,sai dai aka bar megadin gidan yana kula dashi,Satin Daddy daya dadawowa gida sai ga Manajojin kamfanoninsa,dana gidan mansa,dake gida Najeria,sun kawo maza ziyarar dubiyi,da kuma tabbatarmai da zasu rike amanar dake hannunsu,sun nemi ganin Malika,ammh kiri kiri taki Fitowa daga daki,dole suka tafi suna masu tsausayama wannan Ahalin ga Dukiya har Dukiya,ammh ta gaza yi musu mganin damuwarsu.

    Tsakaninnsu kwana biyu sai ga wakilan Hannayen jarinsa na kasashen ketare,mrs Suzan da Mr john Abraham,Sunzo duba jikin Daddy tare da rokon Malika ta dawo su cigaba da huldar kasuwansunsu tare,domin suna jin dadin harka da ita,tun kafin Daddy ya basu amsa Malika ta basu,ta sanar dasu bazai yuyu ba ita yanzu bata da sauran wani motsi ko wani Dubara aduniyarnan,kawai su cigaba da gudanar da komai,ga waya sai su dinga tattaunawa,ammh malika bata ko sha”awar Fita yanzu domin tana ganin Tabbas duk randa tafita sai ta samu masu Nunata suna mata dariya.

    Ayanzu haka tarage shigar banzanta,ammh bata iya saka kayanmu na hausawa,sai dai ta sanya dogayen Rigana,irin na kamfanin Armani,sai ta saka gyalen doguwar rigarta ta yane kanta dashi,bata cin Abinci sosai,sai in Daddy ya matsata,shiyasa wani lokacin tafi son ta Wuni daki ta kwana bata Fito ba,sai dai in Daddy yagaji da cigiyarta ne sai Hajiya ta leka ta kirata,Abinci ko wani lokacin yadda su Dose suka jera haka zasu so su dauka,sai ta Wuni bata sa komai cikin bakinta,don ita ayanzu tafi kaunar mutuwarta Fiye da komai,don gani take tatashi A malika malik dinta ta koma Malika kawai.

    Dr Abbas,shine Amintattacen Likitan Su Malika,tun tuni,toh bayan dawowarsu gida shi ya rinka zuwa yana duba Daddy agida duk bayan kwana,shiya sanar dashi ya daina zama adamuwa ya rinka samun abokin hira,yadaina zama shuru,shiyasa yanzu zaka ganshi zaune afalonsa, yayi tagumi shuru shi kadai,Hajiya binta ko wani lokacin take zama,dashi in ko tatafi kichen sai dai ya zauna shi kadai.

    Ganin haka yasa malika tadinga daurewa tana zama dashi,ammh wani lokacin sai dai yayi ta mganarsa bata cewa uffan,daga eh sai A’a,daya mtsamata da Nasihan tayi hakuri,sai dai kawai yaga tana share kwallar kuka,sai ya kyaleta sai dai ka gansu sunyi zugum,ba mgana shi Alhaji Abdulmalik takaichinsa Daya ko azakar din nan bai iyaba,balle aje ga karatun alqur”ani,balle ya dinga karantawa ko azuciyarsane,shiyasa sai dai ka ganshi yayi zura gwanin ban tsausayi,toh balle ita yarsa tasa,da bata san komai na addini ba.

    Gabadaya Malika ta tsorata da Abunda Saleem yayimata ko barci take ta dinga mafarkin Abun kenan,haka zata farka tana kamkame jikinta tana Fizge fizge tana bashi hakuri,Sai daga baya ta gano mafarki,kuka kuwa tayishi kamar idonta zai tsiyaye in tatuna yau wai itace bazawara,Abun na mata ciwo sosai,shiyasa suna ko mai harafin S taji an ambata sai ta zabura ta tsorata,balle a ambaci sunan Saleem kai tsaye yanzu zaki ga ta fara makyarkyata tana hawaye,Idanuwanta suna nuna tsoro kara kara,shiyasa ta haddace kaminshi tsab,kamar yadda ko ya Fada Yadda bazata manta Abunda yayi mata ba ,To tana jin har abada batajin zata manta muguwar Fuskar *SALEEM KABIR KUMO*

    Sai ga Malika,yanzu duk wannan ji da kan da rashin kunyar datakema Hajiya binta bashi,tsakaninta da ita yanzu sai gaisuwa,yau an wayi gari Malika zata kalli Hajiya binta tace mata ina kwana,duk da daga nan bata kara cemata komai,ammh ko ba komai An samu cigaba sosai,haka da Joda tadawo,wlh ganin yadda Malika Takoma sai da tayimata kwallah,ada bata tsausayin Malika ammh dole duk wani mai imani ya tsausayamata,shiyasa itama taji kawai ta tsani ma Saleem gabadaya Tun sanda ya ketama Malika haddi,bana irin yadda addini ya koyarba,sai ta hanyar karfi kamar wani dabba

    Ita ke zama da ita koda bazasuyi dogowar hira ba,mutum ma rahama ne,kuma Afuskar Malikar zaka Fahimci tana jin dadin zama da joda sosai,haka joda zata dage tayi ta bata lbrin rayuwarsu ABU chika da suka je pratical,itako tana Saurarenta sai dai kawai taga ta murmusa alamar tana jin dadin zama da ita sosai.
    ___________________

    Lokacin da Ya marwan yaga sakon Saleem,tsaki yaja ya Fice ko amsa bai bashi ba,sai dai ya kira Abbi ya sanar dashi Abunda Saleem din yace,yaji dadin hakan duk da bai nunama Marwan din ba,ammh shi ya Fahimci hakan..

    Abbi bai yarda al”qawari ba lokaci bayan lokaci yana zuwa ya Duba Daddy,su Wuni suna shan hiransu,wani lokacin in yazo har yatafi baya saka malika a idanuwansa,wani lokacin ne takan Fito su gaisa sama sama ta koma daki gwanin ban tsausayi,Duk da yanzu tana kokarin sallah akan lokaci,sai dai Abunda ta gaza samu wanda zai zaunar da ita ya koyamata addinin da kyau shine bata dashi,sai dai kawai Abunda ta iya takeyi,sallan nata ma ba cikakka takeyi ba,balle in ta idar tana son yin addu”a akan Halin data ke ciki,ammh bata iya ba,sai dai ta zauna tayi zuru tana sharan kwallah,tana fadin aranta Allah ya sakamata kawai.

    Shiko Saleem,tundaga wannan sakon bai kara turama kowa sako daga gida ba,duk da yaga Ya marwan din ya bude sakonsa,ammh ya Fita batunsa bai bashi amsa ba,bai damu ba dama burinsa sakon ya isa ga Abbi,kada sai ya koma gida Abbi ya batamai rai Fiye da yadda shi ya bata mishi.

    Shiyasa ya maida hankalinshi kan Abunda ya kaishi yana kokarin yagama komai kafin ya koma gida ya Tunkari Abunda ke gabanshi,domin yasa tabbas,zai Fuskanci barazana daga iyayensa nasa,wadanda suka dauki Fushi dashi sosai akan lamarin Yarinyarnan,koma menene ya Shirya tsab wlh ko da anshashi dole ya zauna da yarinyarnan,Tohpha sai ya kara amfanin da wannan damar domin Ninka ramuwarshi gareta.

    *

    *AFTER 2 MONTH*

    Kwance tace bisa makeken gadonta ta dunkule cikin blanket,tana ta rawan sanyi domin kana jin yadda hakoranta ke bugan juna,Tun kwana biyu da suka,wuce takasa gane kanta,kwana take da zazzabi ga tashin zuciya,kuma sometimes tana Fama da taruwar miyau abakinta,ga kasala da yawan Mutuwar jiki,barci ko bata gajiya da yinsa,tarasa wazata fadama damuwarta ne,Ko jiya Da hajiya ta ganta sai da ta tsaya Shuru tana kallonta kafin ta tambayeta meke damunta,yamutsa fuska tayi kafin tace itama bata sani ba,kuri tayimata da ido kafin ta kada kai kawai ta Wuce batace komai ba,ammh cikin ranta gabanta yana bugawa kada Allah sa hasashenta yazama gaskiya.

    Yau Abun yayi tsanani don dakyar ta iya tashi tayi sallar Asuba,ta koma zazzabin ya rafketa,ganin har karfe 10:00am na safe bata Fito ba,toh a kidanta gari na waye zata Fito taje Falon Abbanta inda yake xaune bisa kekensa ta gaisheshi,su dan taba hira kafin ta koma daki,ammh yau ko Duriyarta baiji ba,shiyasa ya damu yama hajiya binta mganar don Allah ta Dubomai Bby tana lafiya kuwa?..

    Ita ta shiga da kanta har dakin nata,ta iske su Dose suna ta gyaran Falon,gaiaheta sukayi ta amsa tana tambayansu ina Malika,nan suke sanar da ita Madam,tun jiya bata Fito ba kada kai tayi,kafin ta tura kofar bedroom din ta shiga da sallama,Sai dai ta dade tsaye tana dube dube kafin ta hango malikar kundundune cikin bargo tana makyarkyata,da hanzari ta karisa gareta tana Fadin”Malika…”Take Fada tana zama kusa da ita,

    Jin Shuru yasa ta yaye bargon jikinta tana Fadin”Lafiyanki kuwa yau shuru….Ashhh..!Mganarta ta katsene sanda ta taba goshinta taji zafi rau,waigowa Malika tayi tana rike bargon jikinta na rawan Sanyi tace’Banda lafiya ne Hajiya Tun jiya da daddare…”Hajiya binta tace”,Wayyo sannu bari naje na sanar da Alhaji dama shi yace na duboki yajiki shuru,ammh ki tashi kiyi wanka ki karya kafin nayima Dr Abbas Waya..”Da kai ta amsa kafin takara dunkulewa cikin bargon.

    Hajiya binta tadade tsaye tana kallon Malika kafin ta Fice daga bedroom din,Su Dose ta umarta dasu hadama Malika Ruwan wanka itama Merry tace mata ta sauka kasa,taje kichen ta amso breafsat din Malika,awajen Atika da toh suka amsa kafin kowacce Ta nufi inda aka sata.

    Koda Hajiya binta ta sanar da Daddy hankalinshi ya tashi jikinsa na rawa yace ta kiramai Dr Abbas tace yazo da hanzari Babby ba lafiya, hajiya na sanar dashi yace gayinan ahanya zashi asibiti ammh gashinan zuwa.

    Tagumi yayi yana Fadin”Haba shiyasata najita shuru,meke damunta ne Binta..? ajiyar zuciya ta sauke kafin tace”Zazzabi ne inaga,don jikinta yayi zafi sosai…”Girgiza kai yayi yana fadin”Binta zuciyata takasa natsuwa taimakamun zuwa dakin Baby don Allah..”Bata yi gaddama ba ,ta isa bayanshi tafara turashi zuwa dakin Malika.

    Koda suka shiga harta fito wankan,ta shirya cikin wata doguwar riga,ta koma ta kwanta tana nishi,Hajiya ce ta shiga ta rikota suka Fito falo ta kwantar da ita kan kujera,Daddy ya karisa gareta yana kan kekenshi yake fadin”Sannu Babyna…”Dakyar ta dago tana kallonshi hawaye suna gangaromata,bata iya amsawa ba,illah rarrafowa datayi ta kwantar da kanta bisa cinyarsa tana nishi dakyar.

    Hannu yasa ya dafa kanta yana jin yadda jikinta ya dau zafi sosai,Shafa kanta yake yana jeramata sannu,kafin ya kalli Hajiya binta yana fadin”Binta nace ko zata ci wani abun ne kafin Dr Abbas yazo,kila yace zai maka allura ma..”gyada kai Tayi kafin tayi mgana ma merry dake gefe ta shiga kwaso kulolin data dauko da kasa tana jerawa gaban Alhaji Abdulmalik,wacce malika take kwance kan kafafunsa,rabin jikinta na kasa tana nishi sama sama.

    Dakyar Daddy ya iya lallabata ta sakeshi ta zauna ta jingina da kujera tana yamutsa fuska,tunda aka bude Ferfesun kayan cikin,taji zuciyarta na tashi,ta kauda kai tana wani toshe hanci,mamaki ya kama Daddy ya kalleta yana Fadin”Bby menene…? Kuka ta fashe dashi kafin tace”Daddylove zuciyata tana tashi adaukemun shi daga gabana,inaji kamar zanyi amai…”

    Da Sauri ya umarci merry data Rufe kolan kafin ya kalleta yana Fadin”To an dauke yanzu me zaki ci,ta hada miki tea,…? Gyada kai tayi duk da batason cin komai,ammh bata so tabar Daddynta yana zama cikin worry akanta.

    Tea din ta hadamata ta mikamata cikin wani kofin glass,mai kyau karba tayi tafara kurba ahankali,ko Kurba uku batayi ba tafara jin zuciyarta na tashi,tayi saurin mikama merry Kofin bata kai ga mgana ba,taji Daddy na Fadin”Haba Babby ki daure kisha mana,ga Dr nan zuwa yanzu sha kigani…”,tana so tayi mgana Abun takasa saboda yadda madarar ke taso mata,amai taji ya zomata da karfi ko kafin ta mike tafara kelayashi awajen cikin kayan abincin dake gabanta.

    Daddy yace”Subhannallah..,Binta kamata karta fadi…”Da sauri Hajiya ta karisa tana riketa tare da jeramata sannu,sai da ta amaye dan shayin data sha tas,kafin wani ruwa ruwa ya biyo baya yunkuri take,ammh komai baya Fitowa saboda babu komai acikinta,shiko yana gefe yana jeramata sannu kamar zai mata kwallah Fadi yake”Kai wai ina Dr Abbas ya tsaya ne..? yake Fada cike da damuwa.

    Sai da tagama kafin tayi baya jikinta babu karfi hawaye suna Fita daga idanuwanta,Saboda yunkurin aman har Fitsari tayi awajen duk ta bata rigar dake jikinta,Kan kujera Hajiya ta kamata ta kwanta tana maida numfashi,su kuma su Dose suka fara kokarin kwashe kololin da ke wajen ita kuma ta dauko Abun goge goge, tafara goge wajen,suna cikin hakane Dr Abbas ya kira wayar Daddy yace gashi awaje.

    Hajiya binta tasauko taje ta mai jagora har zuwa sama Falon Malika,inda sukayi musabaha da Daddy yana tambayanshi ya jikinsa,amsamai yayi da”Jiki yayi sauki,don Allah Dr Bby zaka dubamin tun jiya take fama da zazzabi,yau da safe kuma jikinta yayi zafi,yanzu haka ka ganta nan amai tagama..”

    Yafada yana nuna mishi ita,Jinjina kai yayi ya karisa gareta,durkusawa yayi gabanta yayi yana Fadin”Sannu Madam,…”Dakai ta amsa idanuwanta na lumshe,ita kadai tasan halin data ke ciki,kallonta yayi yana nazarinta kafin yace”Plz madam,ko zaki iya tashi,saboda na dubaki da kyau…”jin haka yasa tafara yunkurin tashi da sauri Daddy yace”Don Allah Binta taimakamata…”Yafada yana Tura keken nashi zuwa gaban Malika.

    Ita ta riketa tatashi zaune bayan ta jingina da cussion din kujera tana maida numfashi,mikewa yayi kafin yadan rankwafa,yasa hannu ya dalle mata ido duka biyun,yana kallo kafin ya saketa,ya koma ya riko duka tafukan hannuwanta yana kallo kafin yace”Arm madam plz yaushe rabonki da ganin period dinki..? Bude ido tayi ahankali tana kallonshi kafin ta bude baki ta kyar tace”2 month kenan,+ dis month shima ban gani ba haryanzu,kuma date dina 16 ne.. “Tafada tana yamutsa fuska.

    Gyada kai Dr Abbas yayi kafin yace”Is ok bari na Dibe jininki na tafi dashi lab,su auna buh ina kyautata zaton madam u are pregnant…”Gabdayansu suka raazana da jin wannan mganar daga bakin Likitan,Daddy ne ya zaro ido yana kallon Hajiya binta,wacce tayima Malika kuri,domin dama zuciyarta tun shekaran jiya take hasasomata Allah yasa Malikar ba ciki ne da ita ba.

    Itako Malika tana da kishingide sai gata zaune digigir da kanta idanuwanta duka awaje tana Fadin”Dr Wit pregnant,plz stop dis joke don Allah…”Tafada cikin tashin hankali,da Sauri Dr Abbas yace”No bani da tabbas,buh duk wasu symtoms na masu juna biyu ya bayyana atare dake,so yamzu mu bari har na kai jininki zuwa lab,su auna su gani….”Ya fada yana bude wani karamin akwati daya zo dashi.

    Siranji ya dauko tare da allura ya hadasu waje daya,ya riko hannunta ya dibi jininta,kafin ya sanya mata auduga ya danne wajen yana jeramata”Srry..Srry….”yana gamawa ya maida komai cikin dan akwatun nashi ya mike yana fadin”in na tashi aiki kafin na wuce gida,zan biyo na kawo muku result din…”Godiya Daddy yayi tamai kafin su sake musabaha ya fice yana Fadin”,Allah kara lafiya Madam….”

    Koda Dr Abbas ya fita ba wanda ya samu zarafin magana,banda shesshekan kukan Malika daya cika dakin,Daddy ko kansa ya sunkuyar yana jin kamar zuciyarsa zata Fito waje saboda yadda take harbawa.,Hajiya binta ko na zaune gefe tana girgiza kai kafin tace”Sai hakuri Alhaji,ammh tabbas ko ni naga alamun Shigan karamin ciki atare da malika,bandai yi mgana bane saboda ban tabbtar ba….”

    Dagowa Yayi idanuwansa jawur yana fadin”Ciki kuma binta,innalillahi ina Bby zata kai ciki awannan halin datake ciki…”Yafada yana kallonta,gyada kai hajiya binta tayi tana Fadin”Haihuwanshi zatayi Alhaji,toh zamu zubar da Abunda yake da shakikin mahaifi na sunnah,ai da an tabbatar da cikin ka kira Kabir kumo ka sanar dashi Abunda ke Faruwa,nasan suma bazasu ki karbanshi ba,tunda dansu ya digashi…”

    Ajiyar zuciya ya sauke yana jinjina kai alamun gamsuwa da mganarta,kawai basu ankara suka ga Malika ta mike tana tsalle bisa kujera tana dukan cikinta tana kuka da ihu kamar wata mahaukaciya tana fadin”Bani son wlh bazan haihu ba,zan kashe kaina wlh…”Take fada tana buga jikinta da duka hannuwanta biyu tana kuma tsalle atare…..

    Da hajiya binta Da Daddy dake kan keke ba”a san wanda ya riga wani ba,shidai Daddy ji yayi kafarshi na rawa kokarin mikewa yake ammh yakasa saboda yanayin jikinsa komawa yayi ya lafe bisa keken yana Fadin”Binta taimakeni ki riketa kada tama kanta ta lahani, Wayyo Allah!…? yafada wasu kwallah na zuraromai,…

    Dakyar Hajiya binta ta riketa,rumgumeta tayi tana kuka mai cin rai take fadin”Hajiya ya zanyi…? me zanyi kuma? Hajiya ki sanar dani wata addu”a akeyi mutum ya mutu ya huta da wannan Duniya da babu komai cikinta sai bakinciki,…”Take fada tana kamkameta cike da tashin hankali,

    Rumgumeta hajiya binta tayi wani tsausayinta na Tsirgamata tace!”Ki daina Fadin Haka,babu wata addu”ar mutuwa aduniya sai dai Addu”ar da in wani bala”i ya kusanto ka sai ka karanta,ki maida kukanki ga Allah Malika,don bazaki iya chanza kaddaranki ba,kiyi ta karanta *INNALILLLAHI WA”INNA ALAIHIRRAJU’UN*…Insha Allahu zakiji sauki azuciyarki…”

    Ahankali ta shiga maimata kalmar asarari,tanayi tana zubar kwallah,Hakama Daddy dake gefe shima tayata maimatawa yake yana sharan kwallahn shima,Malika ne ta kalleshi taga yana kuka,saboda tsausayinshi da kaunarshi bata san sadda ta saki hajiya ba,tatafi gareshi ta fada jikinsa tana kuka harda sheshaheka tana Fadin”Am srry Daddy,plz stop carrying,i love u, i dont want to lose u…..”

    Take Fada tana zame kanta bisa cinyarsa tana kuka da duka karfinta,Kanta yake shafawa har zuwa bayanta,hawayensa suna gangarowa zuwa Kanta yake Fadin”Nabari Babby,ammh nima ki taimakeni kada ki kashe kanki,in kika aikata haka wlh zan zama gafaalle,aduniya kuma asararre aranar gobe kiyama…”Damke hannunshi tayi tana Fadin”Am wit u Forever and every Single day of Forever Daddylove,plz Forgive me….”Take fada muryanta ciikin kuka.

    Hawaye yake share mata itama tana sharemai,Hajiya binta dake tsaye gefe,itama kwallar ta share tana jin kamar tayima Malika da Alhaji kuka mai yawa,yau din da suka bata tsausayi Fiye dana kullum.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!