Search
You have no alerts.

    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
    Da gaske ciwon kai ke damun Taj saboda bai iya sanya abu a rai ba. Ya so ƙwarai ya ja Abban Hamdi a jiki. Ba don neman soyayyarta ba, wannan da kansa zai yi ba ya buƙatar taimakon kowa sai Allah. Mahaifinsa yake son nunawa a rayuwa kowa da ƙaddararsa. Kuma a kowacce sana’a indai ba addini ne ya haramta ta ba, akwai mutumin banza da nagari. Don al’ada ta ƙyamaci wani abu ba shi yake nufin yinsa laifi bane. Sannan uwa uba akwai uzuri ga ƴan Adam domin ba kowa ke dawwama cikin saɓo ba.

    A ganinsa rashin aikin Abban Hamdi wata hanya ce ya samu da zai iya sako shi cikin tasa sana’ar. Idan Allah Ya sanya musu albarka kasuwa ta buɗe Alhaji zai iya fahimtar kowanne bawa akwai hanyar arziƙinsa. Sannan ko iyaye ba sa so indai Allah bai haramta ba sannan ɗan bai kasance mai saɓawa kowa ba, albarka za ta iya binsa duk inda yake.

    Ƙarar wayarsa ce ta tashe shi daga kwanciyar da ya jima yana yi. Sunan Salwa da ya gani ya sanya shi yin tsaki. Ita bata san gudunta yake yi ba? Har yau yana mamaki da bata yi tunanin kamar yadda mata ke killace kayansu na ciki haka kowanne namiji da ya san mutumcin kansa yake yiwa nasa ba. A iya saninsa ƙiwa da rashin son aikin namiji ba zai sa ya bawa ƙanwarsa shaƙiƙiya wankin ƙananan kaya ba. Ballantana kuma wadda babu wani abu da ya haɗasu.

    Bari ya yi kiran ya katse sannan ya kirata.

    “Don Allah ka buɗe min ƙofa na manta muƙullina a ciki.”

    Falo ya fito sanye da dogon wando na sanyi ruwan toka da farar shirt. Ya buɗe mata jamlock ɗin ya juya zai koma ɗaki sai ta kira sunansa.

    Tun ranar da ta gyara masa ɗaki da faɗan da Ahmad ya yi mata ta rage kuzari da karsashi a komai. Fargabarta ita ce ɓacin ran da ta gani tare da Taj da kuma shawarar da Ahmad ɗin ya bata akan ta cire shi daga ranta. Da za ta iya da tun kafin ta zubar da ajinta ta cire shi ta ƙarfin tsiya tunda ta fahimci bata gabansa ta fuskar da take so.

    Sake kiransa tayi da bai juyo sosai ba.

    “Ya Taj don Allah ka yi haƙuri akan abin da ya faru rannan. Na fahimci kuskurena.”

    “Ya wuce, kada ki damu.”

    Fasa tafiya ya yi da ya tuna ƙanwar Ahmad ai ƙanwarsa ce shi ma. A matsayi guda duk su biyun su ke zaune a gidan. Shi yasa yaga dacewar ya bata shawara.

    “Ko don gaba ki kiyaye irin wannan. Ba ni ba, ko Yaya ki ka wankewa undies bana jin za ki burge shi.” Kai ta sunkuyar sai ya yi murmushi “ku mata ba kwa son a taɓa koda jakarku. So just imagine ace ni nayi miki wannan karambanin. Will you realy be happy that I helped?”

    Kunya maganar tashi ta bata. Ta rufe ido ta shige ciki da sauri tana mayar da numfashi. Da tunanin yadda ya yi maganar a tausashe ta ƙarasa ɗaki. Sai da cire kaya za ta shiga wanka ta kuma tariyo zancen sai taji faɗuwar gaba. Shin magana ya yaɓa mata ko kuwa ya sauko ne?

    Domin tabbatar da matsayin maganar da sai ta tura masa SMS da yamma da ya fito falo suna hira da Ahmad. Daga kitchen ta leƙo bayan ta tura tana kallonsa ya duba saƙon, ya kuma rubuta reply. Da wani irin sauri ta koma ciki ta buɗe. Nata ta fara bi inda ta rubuta masa saƙo kamar haka.

    (Ya Taj nagode kuma ina mai sake baka haƙuri. If I am forgiven please give me a chance to be your friend.)

    Shi kuma ya rubuta wannan amsar.

    (Kada ki matsawa kan ki da son neman wani relationship dani bayan already akwai. Ƙanwar Yaya Ahmad ƙanwar Taj ce.)

    Ranar da ƙyar ta gama girki. Saƙon dake cikin amsarsa ya fito ɓaro ɓaro. A matsayin ƙanwa kaɗai ya ɗauketa. Daga yau za ta gwada cire shi daga zuciyarta. Sai dai abin da wuya domin son bai yi shawara da ita ba ya yi mata kamun kazar kuku.

    ***

    Faɗa Yaya take kamar ta ari baki a waya. Sajida da Zee su ka matsu ta gama ta basu labarin me ya faru. Sun dai fahimci Hamdi ce tayi wani laifin. Ita kuma Anti Labiba da su ke wayar banda dariya babu abin da take yi.

    “Abin dariya ki ka ɗauki abinnan Labiba? Wace ƴar arziƙin ce za ta guji girki kamar ba mace ba?”

    “Yaya ki barni da ita don Allah. Na faɗa miki ne fa kawai saboda kada ku ji shiru bata dawo ba. Zan ɗan riƙeta ne in sauke mata gammon da ta ɗauka.” Cewar Labiban tana murmushi.

    Yaya ta gyara zama tana hararar masu matsowa jikinta don son jin me ake cewa “amma fa samun wuri ne. Bata taɓa gwada min wannan shegantakar a nan ba. Iyaka dai in tana gida girki ya faɗo kanta tayi ta cika tana batsewa kenan. Ita a dole bata son sana’ar uban da yake wahaltawa rayuwarta.”

    Haƙuri Anti Labiba ta bata “ki barni da ita kawai Yaya. Girki kuma tunda ta iya ai magana ta ƙare.”

    A haka su ka yi sallama bayan ta sake roƙon alfarmar kada Yaya ta yiwa Hamdi magana idan sun yi waya. Ƙarfe uku bayan yaranta biyu sun tafi islamiyya ya rage jaririyar da take goyo da yayarta mai shekara biyu da rabi. Ta fito abinta cikin shiri ta sami Hamdi a falo tana kallo.

    “Hamdi zan fita amma ba jimawa zan yi sosai ba. Ga kaza can na fito da ita ki yi pepper chicken kafin na dawo. Sai ki haɗa coleslaw. Na riga na dafa jallof ɗin shinkafa.”

    Jin abin da ta ce ba shiri ta kashe TV ɗin.
    “Anti ni zan girka?”

    “Kina nufin zancen da mu ka yi jiya da gaske ki ke?” Anti Labiba ta ƙanƙance idanu.

    “Anti wallahi ni…”

    “In fasa fitar kenan komai mahimmancinta in ƙarasa girki ko?”

    “A’a Anti. Amma naga tattali ma yana da kyau. Tunda anci kifi da rana a bar kazar sai gobe.”

    Ƙiris ya rage Anti Labiba ta fashe da dariya. Fuskar Hamdi na nuni da cewa da gaske take. Lallai idan ta biye mata ba za ta sami biyan buƙata ba.

    “Abbansu ne ya aikeni. Gashi kuma yana hanya tare da abokinsa. Na zata ke me fitar dani kunya ce…” ta sauke mayafinta “nagode da ki ka nuna min ban isa ba.”

    Jikin Hamdi rawa ya fara. Bata son ayi fushi da ita ko kaɗan. Musamman mai kyautata mata. Da sauri ta bar falon ko kallon Antin ta ta bata kuma yi ba ta shige kitchen. Anti Labiba ta ƙunshe dariyarta ta fice.

    Bata zame ko ina ba sai bayan National Military Cemetary da an ɗan wuce National Stadium a nan cikin umguwarsu Karon majigi. Wurin aminiyarta Hauwa taje don nan ne take da tabbacin za ta juyawa jin kunya baya. Daga bakin ƙofa su ka rungume juna saboda sun ɗan kwana biyu basu haɗu ba.

    “Sannu da zumunci Labiba. Ina ta waƙar sake zuwa ganin baby amma kwanakin nan orders suna neman fin ƙarfina.” Cewar Hauwa tana karɓar goyon Anti Labiba.

    “Mu ai haka muke so. Ɗan kasuwa baya kiran yawa. Ki dai ce kasuwa tayi albarka ki kuma godewa Allah.”

    “Alhamdulillah ala kulli hal.”

    Hira su ka ɗan taɓa sannan Labiba ta faɗi abin da ya kawota.

    “Ni kuwa kina ɗaukar ɗalibai ki koyar dasu?”

    “Ban fara ba amma na gama duka shirye shiryen da ya dace. Nan da ƴan kwanaki za ki ji sanarwa.”

    Anti Labiba ta saki jiki “Masha Allah. Nayi sara akan gaɓa. Dama ƙanwata nake son kawo miki. So nake ta goge sosai a harkar snacks ɗin nan ita ma.”

    Hauwa ta ce “akan ƙanwarki ki ke tambayar class dama? Ai kin san ko bana yi dole na koya mata.”

    “Allah Ya ƙaro kasuwa. Nagode sosai.”

    “Babu komai. Ai yiwa kai ne.”

    Hirarsu su ka cigaba da yi inda Labiba take ta koɗa daɗin kayan ciye ciyen da Hauwa ta ajiye mata. Da za ta tafi ta sayi frozen samosa.

    *

    Da yake babu wani abu da zai ɗauke mata hankali, bata wani jima ba ta gama ta gyare kitchen ɗin. Tana jin an taɓa ƙofa kuwa ta soma murmushin neman shiri. Ita kuma Anti Labiba sai da ta zo bakin ƙofa ta daina fara’a. Fuska a cinkishe ta shiga gida.

    Hamdi ta shiga damuwa. A irin miskilancinta ɗaki za ta tafi amma ita shaida ce. Ganin ɓacin ran Anti Labiba na nufin anyi mata abin da ya ɓata mata rai sosai.

    “Anti zo ki gani. Na gama.”

    “To an gode.” Ta bata amsa ko kallonta bata yi ba.

    Fuskarta canjawa tayi kamar tayi kuka ta ce “Allah na daina Anti. Ki yi haƙuri.”

    Ledar pack ɗin samosan ta bata ta ce ta soya. Wannan karon ko kaɗan bata nuna komai na rashin jindaɗi a fuskarta ba. Da ta gama Anti Labiba ta ce ta ci ta faɗa mata ko da daɗi.

    Tunda ta gutsira ta kama murmushi.

    “Yayi miki?”

    “Da daɗi sosai.”

    Sai lokacin Anti Labiba ta saki fuska ita ma tayi murmushi.

    “So nake ki koma gida da sana’ar hannu. In sha Allah nan da kwana huɗu za ki fara zuwa wurin Hauwa koyon waɗannan abubuwan.”

    Farinciki sosai ta gani a tare da Hamdi. Ta dinga dariyar yadda ta canja lokaci guda.

    A zahiri tana yiwa ƙannen nata uzuri idan su ka nuna ƙyamar wani abu na Abbansu. Maganar gaskiya duk kirkinsa akwai abin da fa dole ya tsayawa mutum a rai. Ƴaƴa yawanci babu ruwansu da talauci ko arziƙin iyayensu. Indai akwai jinƙai da kulawa a tsakaninsu za ka ga suna ƙaunar abinsu da zuciya ɗaya. Amma duk lokacin da kaga ƴaƴa na kunyar nuna iyayen a wasu wuraren, za ka samu nakasu ta wanni fannin. Inma dai daga ɓangaren ƴaƴan in aka samu marasa godiyar Allah, ko kuma daga iyayen idan sun shuka wani abin da zai kunyata yaransu.

    Ga dai shekaru sun ja. Amma har yanzu kallo ɗaya ya ishi mai idanu gane waye Abba Habibu. Irin haka ne abin da ake gudu. Kayi abu ka barshi amma tasirinsa ya gagara barin rayuwarka komai tsahon lokaci.

    ***

    Kwana biyu Kamal ya ɗauke ƙafa daga gidan Ahmad. Taj ya ƙule iya ƙulewa. Kuma ya naɗe ƙafa ba ya zuwa site ɗin aikinsu. Kamal ɗin kaɗai ke zuwa ya wuni yana monitoring komai. A rana ta uku ne ya gaji da gudun rigimar da za su yi da Taj akan zuwansa gidan Abba yaje gidan Ahmad ɗin. Bari ya yi sai gabanin azahar lokacin da ya tabbatar yayan nasu yana wajen aiki sannan yaje.

    Babu kowa a gidan sai Taj da Zahra dake kitchen. Fitowa tayi su ka gaisa sannan yaje ƙofar ɗakin Taj. A rufe take, ya yi sallama sannan aka buɗe.

    Taj bai jira shi ba ya koma ya zauna akan gado ya cigaba da aikin da yake a laptop ɗinsa.

    “Wai nan gaba kake dani?” Kamal ya faɗi da sanyin jiki.

    “Kai zan tambaya da ka daina zuwa gidan nan.” Taj ya mayar masa rai a ɓace.

    Tausayinsa Kamal yake ji. Bayan abubuwan da yake rayuwa yana haƙuri da rashinsu, baya jin zai juri wani abu ko yaya yake ya haɗa su rigima ba. Zai fara bashi haƙuri sai aka kira Taj ɗin.

    Abinka da sabonsu na rashin ɓoyewa juna komai. Gaisawa kawai su ka yi da Amma ta sako zancen Anisa. Ya kunna speaker ya yafito Kamal da hannu.

    “Taj kana ji na kuwa?”

    “Ina ji yanzu Amma. Me kike cewa?”

    “Maganar Anisa. Kai baka ce min komai ba. Na share don ina zaton sai ka dawo za mu yi magana. To jiya Hajjo ta kira ta ce za ka wulaƙanta mata jika. Idan ba ka so ka faɗa ta samo mata wani.”

    Hannu Kamal ya dinga juyawa yana son sanin me take nufi.

    “Amma da kin bari na dawo dai.”

    “Ai ka san halinta. Yanzu sai ta juya zancen. Ba ka son Anisan ne?”

    Ƴar dariya ya yi daga ji bata kai zuci ba. Baya son karɓar abin da zai zame masa matsala don ko babu Hamdiyya shi bai taɓa kallonta a matsayin da ya wuce ƙanwa ba. Idan kuma ya ce baya so nan ma duk wanda ya san tarihinsa sai ya zage shi.

    “Wa zai ƙi mace kamarta?”

    “Wannan wace irin amsa ce?”

    Sarai ya ji ɓacin rai a cikin muryarta. Ya kalli Kamal yana neman agaji. Shi kuma sai ya raɗa masa a kunne cewa ya faɗa mata zai je Abujan su fara fahimtar juna. Haka kuwa ya faɗa mata. Nan da nan sautin muryarta ya koma daidai. Ta dinga shi masa albarka. Bata ga laifin Hajjo ba da take so wa jininta Taj. Da tana da sauran ƴa ma kafin Hajjon tayi masa tayim Anisa za ta haɗa su. Abu guda ne dai ta ajiye a ranta. Idan yaje yace baya so to fa dole a haƙura. Don sun riƙe shi bata so ayi amfani da hakan a matsayin dalilin yi masa tilas. Zai zamana ba don Allah su ka taimaka masa ba.

    Dariyar mugunta Kamal ya dinga yi bayan Taj ya gama faɗa masa yadda su ka yi da Hajjo.

    “Salwa kuma fa? Ko har yanzu ba fahimci ta mato maka ba?”

    “Hmmm, ai baka san me tayi min ba…” ya sake kwashe labari ya sanar dashi.

    Kamal dariya harda faɗowa daga kan gado. Faɗan da su ka manta dashi kenan aka koma hirar masoyan Taj.

    “Yanzu dai da gaske Abujan zamu je.”

    “I’m not interested Happiness. Ina tsoron kada naje su zata na amince.”

    “Sai mu yi mata bayani mu nemi haɗin kanta” ya ɗan kalli Taj ɗin “akwai wadda ka ke so ne?”

    Kamar ya faɗa sai ya tuna reaction ɗin Kamal akan Abban Hamdi kawai ya fasa. Shiryawa su ka yi su ka tafi site tare. A hanya

    “Na fa yi maka laifi Happy. Naje na sake lalata chance ɗin Mal. Habibu ya karɓi aiki da kai.”

    Ana kukan targaɗe, ga karaya ta zo. Taj ya gama sauraron Kamal ya ma rasa abin da zai ce.

    “Kayi shiru” Kamal ya furta yana satar kallonsa.

    “Ka san bana ganganci da rayuwata. Ba don haka ba duka zan maka.”

    “Sai da naje nake ganin kamar ban kyauta ba. Amma ni yadda ya ɗauki zafi da jin sunan Alhaji yafi damuna. Kana ganin ko shi ma yadda yayi maka haka yayi masa? Naji Yaya Hayatu ma yake kiransa.”

    Da daddare Taj ya kira Hajiya ya tambayeta game da Abba Habibu. Don kada ta zargi komai sai ya ce,

    “Hajiya don Allah mece ce alaƙar Alhaji da Habibu ɗinnan?”

    “Me yasa kake son sani?”

    “Don na kiyaye. Kada na taɓa bari girki yasa nayi koyi da irin tasa rayuwar”

    Hajiya na jin haka kuwa tayi masa bayanin da yake nema. Alhaji ya so Habibu tamkar ƙaninsa na jini. A rayuwarsa kamar yadda ƴaƴansa su ke gani yana son kyautatawa duk mai mayar da hankali a harkar ilimi. To Habibu sai dai ace masa gifted. Kana faɗa yake kwashewa. Sai ka rasa wace irin ƙaddara ce ta karkata masa rayuwa ta mayar dashi ɗan daudu. Gashi a lokacin daudancin mafi akasari ba a raba shi da kawalci da sauran alfasha mai zubar da mutumci.

    “Da ya dawo daga Saudiyya yayi ta bibiyar Alhaji yana neman ya taimaka masa da jari ko ya ɗauke shi yaron shago. Amma waccan ƙyama da yake masa tun farkon fara daudun tasa yayi masa kora ta wulaƙanci.”

    Jikin Taj ya yi sanyi sosai. Idanunsa su ka kaɗa su ka yi ja.

    “Bai taimake shi ba?”

    “Inaaa. Ka san shi da kafiya. Tunda ya juya masa baya bai ƙara waiwayarsa ba. Ni dai ƙarshen labarinsa da naji ance ya buɗe shago yana abincin sayarwa.”

    Shiru taji ya yi da tana magana. Ta rage murya,

    “Taj ba za ka sauke naka ƙudurin kayi yadda yake so ba?”

    “Hajiya ba haram bane. Ki cigaba da sani a addu’a. In sha Allah ba zan taɓa yin abin da za ku yi baƙincikin zaɓina ba.”

    ***

    A cikin wata guda mamallakiyar Luciousbites.ng wato Hauwa ƙawar Anti Labiba ta san tana tare da haziƙar ɗaliba. Duk snack ɗin da su ka wuni koya to in sha Allah washegari idan Hamdi tayi kuskure ba zai yi yawa ba.

    Ita babu ƙiwa ko ha’inci, ɗaliba kuma mai ƙoƙari. Aikin nasu yana tafiya yadda ake so. Wasu dama ta ɗan iya sai dai yanzu ta koyi hanyar da ta dace da zamani wurin inganta saninta. Sannu a hankali ta ƙware wajen yin doughnut, samosa, meatpie, springrolls, chinchin irin na ƴan gayu, gashin nama da kifi kala kala. Da kuma uwa uwa haɗaɗɗen plain youghurt, coconut infused youghurt da yogo fura.

    A gida irin farincikin da Anti Labiba ke gani a tare da ita har mamaki take bata. Mijinta ma sai da ya ce wai gani yake kamar an canja ta da wata. Yaran gidan kuwa tunda an yarje mata gwada abin da ta koya, sun kwashi gara ba kaɗan ba. A ci a gida kuma aje makaranta.

    ***

    Wannan wata gudan harda ƴan kwanaki a ɓangaren Taj cikin wahala su ka zo masa. Kacokan ya ajiye aikinsa bayan ya wayar nan da ya yi da Hajiya. Ya karkata akalarsa zuwa ga son lallai sai Abba yayi aiki tare da shi. Kamal da yaga ba zai iya hana shi ba sai ya bashi goyon baya.

    Ranar farko tun safe ya shirya yaje ƙofar gidan Abba. Bai aika a sanar da zuwansa ba. Ya yi zamansa a cikin mota har Abban ya zo fita sannan ya tare shi. Ai kuwa yana ganin shi ya sauya fuska.

    “Baka sami saƙona a wajen ɗan uwanka ba?”

    Gaishe shi Taj ya yi. Bawan Allah yana faɗan ya tsahirta ya amsa sannan ya cigaba.

    “Bana son rigima da mahaifinku. Ban san me ku ka ji game dani ba. Amma ko ma mene ne nufinku ni da Allah na dogara.”

    “Don Allah ka saurareni. Da alkhairi na zo maka.”

    Cikin gida Abba ya koma. Bai ƙara fitowa ba har la’asar. Taj ya tafi amma bai karaya ba. Washegari ma ya sake zuwa. Ranar Abba ko sauraronsa bai yi ba ya wuce ya yi tafiyarsa. A haka su ka cinye sati guda. Wasu kwanakin duk sammakonsa idan ya zo zai samu Abban ya fita kafin ya zo.

    A kwana na tara Taj sai ya canja tsari. Tare su ka zo da Kamal wanda ya ce zai bada haƙurin abinda ya yi kwanaki. A zatonsa ko shi yasa Abban yaƙi sauraron Taj. Yaro ya tura ya ce a faɗawa Abba su Taj sun zo kuma wallahi yunwa suke ji.

    Sajida ce kaɗai a gida da Yaya. Halifa da Zee suna makaranta. Sajida tana jin saƙon yaron ta figi mayafi ta fita. Yaya tana ta kiranta taƙi dawowa. Abba kuwa ƙwafa ya yi.

    “Bawan Allah zamu haɗaka da ƴan sanda wallahi. Bar ganin kuna da kuɗi” ta harare su duka “wallahi muna da masu tsaya mana mu kara daku a hukumance.”

    “Ki yi haƙuri ƙanwarmu. Aiki kawai ƙanina yake son yi tare dashi. Shi ma sana’ar girki yake.”

    “To ya ce baya so. Ai.ya faɗa mana ko ku su waye.” Ta ce da tsiwa.

    “Ɗan tsaya mu yi magana” Taj ya ce bayan ta gama magana. Tsayuwar tayi tana karkaɗa ƙafa ita a dole ranta ya ɓaci.

    Tarihinsa ya bata a taƙaice.
    “I believe yadda nake son in dawo da ƙimata a wurin Alhaji haka Abbanku zai so mutane su yi masa uzuri su karɓi sabuwar rayuwar da ya gina.”

    Cikin mutuwar jiki ta ce “haka ne.”

    “Ina son yin aiki da Abba amma a setting da ya bambanta da wanda ya saba. A inda maza masu yin komai na maza su ke girki. Burina idan an kwana biyu rayuwarsa tayi daidai ta yadda masu aibata shi a bayansa za su ji kunyar abin da su ka yi.”

    Ƙwalla ta saukowa Sajida “zai yiwu? Kana ganin wannan abubuwan na mata za su barshi?”

    Kamal ya sanya baki “Allah aka ce. Ba yadda za ayi ka bar kowa ka kama Shi sannan kasa rai da ganin ba daidai ba. Taj only wants to help.”

    “Mece ce ribarsa idan ya taimaka masa?”

    “Mutane su fahimci akwai sana’o’in da basu keɓanta ga mata ba kawai. Sannan ƙyama ba ita ta dace da irin wanda ya yi rayuwar Abba ba. In an bi hanyoyin da su ka dace shi ma zai karɓu a cikin mutane kamar kowa” Kamal ya sake bata amsa.

    Abin nema ya samu Sajida ta koma gida da murnarta. Abba na ganin hawayenta ya tashi.

    “Me su ka yi miki?”

    Ta fashe da kuka “don Allah Abba ka sauraresu. In sha Allah wannan wahalar neman wurin hayar zai ƙare.”

    Fita ya yi ya sallame su. Taj sai ya ƙi motsawa.

    “Zan sa a nemo min mahaifinka ya zo ya tafi da kai.”

    “Zan tafi amma don Allah ka bani abinci. Yunwa nake ji.”

    Abba ya kallesu. Duk sun yi laushi.

    “Ba ku karya bane?” Ya tausasa murya. Sai muryar tasa ta sake yin ƙasa.

    “Ni dai na sha tea. Happy kuma bai ci komai ba.”

    Abba ya kalli Taj da mamaki “Happy kuma?”

    “Eh. Sunansa kenan” Kamal ya bashi amsa.

    “Yana sallah kuma?” Abba ya tambaya harda matsawa baya.

    Me kuwa za su yi banda dariya. Taj yana yi ya riƙe ciki. Abba ya sami kansa da yin murmushi bayan sun yi masa bayanin sunayen nasu.

    “Innza ku ci ko indomie ce sai na karɓo a shago Sajida ta dafa muku.”

    “Don Allah abinci muke so. Wanda ka girka.” Taj ya ce da sauri.

    Girgiza kai Abba yayi yana ɗan murmushi.
    “Ku jira nayi muku iso a ciki.”

    Sajida ce ta leƙo ta kira su bayan ya shiga ciki. Aka yi musu shimfiɗa a tsakar gida. Yaya ta fito da lulluɓi su ka gaisa. Taj ya dinga kallon gidan yana ayyana wai fa a nan yarinyar nan da ya gani take rayuwa. Yana son tambayar ina take amma dole ya kama bakinsa.

    Abba ya shiga kitchen suna iya hango duka motsinsa ta tagar dake tsakar gidan. Kai kawo kawai yake yi cike da ƙwarewa. Yaya da Sajida kuma suna jansu da hira jefi jefi. Kamal ne kaɗai yake amsawa. Hankalin Taj ya yi kitchen. So yake kawai yaga yadda Abba yake aiki.

    Yaya ce ta lura da hakan ta yiwa Abba magana. Yaran sun burgeta saboda babu girman kai a tare dasu.

    “Nace ko za ka bari ya shigo ciki ya taya ka?”

    “A’a, nagode.”

    Taj ya tashi “gani kawai zan yi. Ba zan saka hannu ba.”

    Sai bayan fiye da minti ɗaya sannan Abba ya ce ya shigo amma iyakarsa ƙofa. Ai kuwa da saurinsa ya shiga. Aikin daɗewar shekaru wato experience yafi aikin iyawa. Taj yaga abin mamaki a tattare da kuzarin dattijon. Ga tsafta don ko ledar maggi babu a ƙasa. Ƙamshi mai rura wutar yunwa ya cigaba da matse masa hanji.

    Fried spaghetti ce yayi musu babu nama a ciki sai busasshen kifi. Ya juye a tray. Sajida ta kawo musu. Sannan ita da Yaya su ka koma falo. Samarin Alh. Hayatu su ka zauna suna zuba santi har su ka cinye.

    Da za su tafi ne Taj ya bashi nambar wayarsu rubuce a takarda.

    “Don Allah Abba kayi shawara.”

    “Naji. Ku tafi.”

    Faɗan nasa bai hana shi raka su har mota ba. Kuma yaƙi tafiya har su ka bar layin. Yana komawa gida ya samu Sajida tana naɗe tabarmar da su ka zauna. A ƙarƙashinta sai ga farar takarda. Ta miƙa masa ya buɗe. Roƙo da magiya ne daga Taj. Sai kuma ƙarin bayani game da restaurant ɗinsa.

    “…idan ka amince za ka yi aiki dani, zan kama mana wuri inda za mu yi developing recipe kafin a gama ginin. Bana son yin business ɗin da zai rushe kafin yaje ko ina. Ka taimaka min..
    Happy Taj”

    Da Yaya su ka zauna shawara. Sai dai washegari da kwanakin da su ka biyo baya kullum sai Taj yaje cin abinci. Har su ka yi masa kwano. Tun Abba yana basarwa har dai ya karɓi tayin da yayi masa. Ba kuma komai ya janyo haka ba sai rasa wurin da zai kafa sana’arsa. Duk inda yaje sai an biyo shi da ƙabali da ba’adi wanda shi ya san gaskiyar dai ita ce ɗan daudu ne. Ba sa ma damuwa da jin ko ya daina. A gida idan yace zai yi kuma akwai iyalinsa da ba zai so mutumcinsu ya zube ba.

    Haka dai bayan kwanaki yana kai gauro da mari ya ce ya amince. Ya kuma duƙufa addu’ar neman taimakon Allah.

    A lokacin kullum Hamdi tayi waya da gida sai anyi mata zancen Taj. Yaya da ƴan uwanta sunansa a bakinsu raɗau. Ita kuwa lamarin bai burgeta ba. Wanda zai zo ya mayar da Abbanta cikin sana’ar girki ba masoyi bane.

    Su Taj da su ka tabbatar sun sami kan Abba sai aka fara shirin zuwa wajen Anisa. Lokacin bai fi kwana goma ya rage masa ya koma ba. A motar Kamal su ka tafi. Da yake ya san gari basu wahala ba da bin kwatance ta google map su ka isa gidan.

    ***

    Aikin snacks da Anti ta ce a tanada saboda zuwan su Taj, Hauwa aka bawa. Hajjo tuni ta fesa musu dalilin zuwan nasa. Anisa sai murna. Sai dai anyi rashin sa’a ana gobe ranar tafiya ta kama ta. A waya ta basu haƙuri ta ce amma akwai ɗalibarta da duk abubuwan da su ka zayyano za ta iya ba tare da sun ji bambancin taste ba.

    “Haɗani da ita” Anisa ta ce don in ba kayan Luciousbites ba, bata ganewa snacks ɗin.

    A waya aka gama komai. Hamdi murna da godiya ta dinga yiwa Hauwa. Ita kuma ta dinga roƙonta kada ta kunyata musu brand.

    Ƙoƙari kam bakin gwargwado tayi. Meatpie, doughnut da samosa su ke so. Sai coconut infused youghurt. Shi ne kaɗai Hauwan ta aiko mata da shi. Sauran kuwa babu komai a ƙasa dole sai anyi. Bayan ta gama ta kira numbar Anisan da aka bata ta sanar da ita an gama komai.

    “To ki bawa mai delivery. Zan turo address.”

    Nan fa ɗaya. Bata san kowa ba. Anti Labiba ma ta dinga kiran mutanenta amma kowa sai ya ce mai delivery baya kusa. Hamdi ta kuma kiran Anisa. Lokacin ita kuma bata jima da yin waya da Taj ba. Yana ƙara neman kwatance. A yadda ta ƙiyasta bai fi minti goma zai kawo su gidan ba. Gashi babu wanda za ta iya aika. Gari an tashi da rashin mai. Duk wata motar gidansu tana layi sai guda ɗaya ta Daddy.

    “Hamdiyya ko za ki ɗauko bolt ki kawo min. Zan biyaki kuɗin tranport ɗin. Fitar ce babu halin yi yanzu.”

    Hamdi ta faɗawa Anti Labiba. Su ka rasa yadda za su yi. Mijin Anti Labiba a wajen gari yake aiki. Ita kuma babu mota. Tayi shahada kawai ta samarwa Hamdi bolt ɗin.
    MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE

    Note
    error: Content is protected !!