Rayuwa Da Gibi – Chapter Twelve
by NadminMASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
Yadda ya gaisa da kowa da zai wuce haka ya tsaya su ka yi musabaha da wanda ya rako su. Sannan ya ɗagawa Taj da Kamal hannu yana ɗan ranƙwafawa kamar yadda ya gaisa da sauran mutanen da su ka gani.
“Ƴan samari barkanku dai. Ya sanyi sanyi? Ya ayyuka? To Allah Ya yi jagora.” Ya dubi mutumin da da ya yi mu su rakiyar ya ce “na barku lafiya.”
“Dakata Mal. Habibu. Waɗannan fa kai su ke nema.”
Tsayuwa ya yi ya sake kallonsu sai dai bai tuna taɓa haɗuwa dasu ba.
“To Allah dai Yasa lafiya” ya ce muryarsa na raguwa saboda rashin sanin ko ba da alkhairi su ka zo ba.
Kamal ne ya amsa masa “lafiya ƙalau.” Sannan ya gabatar da kansa da Taj.
Jin cewa Taj chef ne kuma a yanzu haka ginin restaurant yake sai Abba ya sami kansa da daina saurin zuwa uzurin da ya fito dashi. Zancen bai wuce fita nema ba dama.
“Dama nayi tunanin maganar ba za ta wuce ta ɗaukarka aiki ba. Shi yasa na rako su. Bari na wuce.”
Abba ya yi masa godiya sosai sannan ya nunawa su Taj gidansa. “Ko mu ƙarasa daga soro mu zauna?”
A duk lokacin da ya yi magana sai Kamal yaji zuciyarsa ta karye. Allah Ya sani a yau ya daina ganin baƙin Alhajinsu. Tabbas da wannan rayuwar Taj ya faɗawa da shi ma sai ya yi kuka ba iyayensu ba. Ta yaya zuciya za ta jidaɗin ganin namijin da ya cika a halitta yana irin wannan muryar? Don ma bai san lanƙwasar jikin da sauƙi yanzu ba.
Gidan su ka bi shi. Daga soron ya ɗaga murya yana ta kiran sunan Zee amma sai da ya yi kamar sau biyar su ka ga ƴar budurwa ta fito a guje. Don shi Kamal ji ya yi kamar ya taya shi kiran saboda muryar ba ta tashi yadda ya dace.
“Abba yi haƙuri ban ji ba ne.”
Mutanen da ta gani tare dashi ne yasa ta saurin komawa da baya don bata fito da lulluɓi ba. Ta bayan ƙofa ta gaishe su. Su duka biyun yadda tayi ɗin ya burge su sosai.
“Tabarma za ki kawo da ruwa.”
Bata jima ba ta dawo da hijabi a jikinta ta shimfiɗa tabarmar. Abba ya sake gaisawa dasu sannan ya buƙaci jin neman da su ke yi masa.
“Kamar yadda ɗan uwana ya faɗa maka gidan abinci nake ginawa. To sai na sami labarinka a wajen mutane. Duk da ba haka ake so ba ance ka rasa wurin sana’arka.”
“Eh. Amma yanzu ma haka wani waje zan je dubawa. Idan mun daidaita sai na kama haya.”
Babu wani dogon tunani ko shawara Taj ya ce “hayar kafi so ko za ka iya aiki tare dani?”
“Kai da baka gama gini ba Happy? Zai yi ta jira ne har lokacin?” Kamal ya yi saurin katse shi.
“Me ya kawo ku wurina tsakani da Allah?” Abba ya tambaya da sakin fuska.
“Aiki nake so mu yi tare amma wurin nawa da saura kamar yadda ya faɗa maka. Ina so nayi recruiting ma’aikata da wuri kafin na gama ginin.”
Kamal da ya yi zaton ganinsa kawai su ka zo yi sai yaji hankalinsa bai kwanta ba. Me yasa Taj yake neman abin da zai ƙara nesanta shi da Alhaji? Ina shi ina aiki da wannan mutumin daga jin ance baya aiki?
Abba ya ƙare musu kallo sai ya yi murmushi. Da alama shawararsu bata zo ɗaya ba don yaga irin kallon da Kamal yake yiwa Taj.
“Samari nagode amma ina mai baku haƙuri. Ina da mata da ƴaƴa huɗu. Zama haka a yanzu ma yana damuna balle kuma na wasu watanni. Sannan ina da ma’aikata biyar da har yanzu dani su ka dogara.”
Kuɗi Taj ya ciro daga aljihunsa da sauri.
“Zan fara baka albashi tun yanzu kafin mu fara aikin.”
“Happy!”
Taj ya yi biris da Kamal. Shi kuwa bai barshi ba ya dubi Abba da kyau.
“Kayi haƙuri don Allah. Bari mu tafi.”
Taj ya ɓata fuska “Da gaske nake ina son aiki da shi Happiness.”
Abba sai ya nuna kamar bai ji haushi ba. Yana ƴar dariya ya yi musu godiya kawai ya tashi. Kamal kuma haƙuri ya yi ta bashi sannan ya janye Taj su ka tafi. A mota kuwa kafin su isa gidan Ahmad anyi faɗa kaca-kaca.
“So kake Alhaji ya mutu da baƙincikin ka ko me? Kai yanzu rayuwarka tana yi maka daɗi?”
“Kai baka ji komai ba da aka ce bashi da aiki yanzu?”
“Sai ka taimaka masa da kuɗi.” Kamal ya ce har zuciyarsa.
“Are you serious? Yanzu da aiki da kuɗi wanne ya fi?”
Da wannan cacar bakin su ka koma gidan. Don takaici Kamal ko shiga bai yi ba. A waje ya sauke shi ya tafi.
“Masifaffe.” Taj ya furta yana harar motar.
*
Ikon Allah Zahra ta gani yau tun dawowar Salwa gida. Kwananta shida a Bauchi da aka yi musu gajeren hutum mid-semester. Abin da aka bayar da kwana goma har weekend ya kama shabiyu, a daddafe tayi shida ta dawo. Ƙarya ma ta yiwa mamansu wai field work za su je. Da yake Agricultural Extention take karantawa. Nan kuwa kewar Taj ce ta isheta har tana neman zautar da tunaninta. Abin baƙinciki kuma shi ne tunda ta tafi ko sau ɗaya bai kirata ba. Ita ce ma da ta gaji tayi masa waya harda ɗan ƙorafi.
“Idan mutum yaje gida baya son damu Salwa. Tunda ba daɗewa za ki yi ba gara duka time ɗin ki ya zama na family.”
Ji tayi kamar ya faɗa mata magana. Ta daure ta ce “Ba ka cikin family ɗina kenan?”
“In ji wa? Idan kin dawo zan baki wayata ki gani a yanzu zan chanja yadda nayi saving sunanki.”
Zuciyarta ta harba da wani irin farinciki ta ce “me za ka saka?”
“Ƙanwata Salwa. Yadda nake saving sunan ƴan gidanmu. Manyan kuma ina saka musu Yayata” Kuma bai barta ta gama jin haushin hakan ba kamar shi ys kira ya ce “bari na barki ki huta haka. Sai da safe.”
Azahar a Kano tayi mata. Tana zuwa gidan ko hutawa bata yi ba ta karɓi girkin dare. Zahra tana ta faɗa mata ta jira ayi la’asar amma ta ce gara tayi da wuri tunda tuwo ne. Daga nan ta haɗa juice ɗin abarba, mangwaro da ɗanyar citta saboda ta kula Taj yafi son fresh fruit juice. Da su ta taho tun daga Bauchi.
Bayan tayi sallar la’asar ta shiga ɗakin Taj. Yana ƙullewa idan zai fita amma baya taɓa zare key ɗin. A cewarsa tunda masu gidan suna da kaya a ciki me yiwuwa za su buƙaci shiga idan baya nan.
“Salwa me ki ke nema a nan?” Zahra ta taho da sauri da taji alamun buɗe ƙofar.
Tsintsiya ta sameta tana gyarawa ɗauri. Tana ganinta tayi murmushi.
“Anti Zahra gyara ɗakin zan yi.”
Curiosity yasa Zahra ta ɗan leƙa. Baya buƙatar wani gyara na a zo a gani.
“Yana gyarawa. Ki fito don yayanki sai da ya yi min warning akan bari ke ko mai aiki ku shiga ɗakinsa.”
“Yau ɗaya dai Anti. Ai gara ayi masa gyara sosai. Tunda baya gida zan yi sauri.”
Tafiyarta tayi ta soma da wankin toilet. A sink inda ya tara boxers da singlets da socks ta haɗa komai ta wanke. Sai ta bar masa a bucket yadda zai shanya idan ya dawo. Wankin ma ana yi ana rurrufe ido saboda kunyar da ta dinga ji. Ɗaki ya fito fes dashi don har bedsheet sai da ta canja masa. Bayan ta gama komai ta rura gawayi akan gas cooker ta wuce da robar turaren wutan da ta siya online. Tun Zahra na bin ta da ido har tsananin mamaki yasa ta koma cewa ‘uhmmm’. Yau ko ɗakin miji ne aka yiwa haka ai dole ya yabawa matar balle wanda a iya saninta babu soyayya a tsakaninsu.
Ahmad ne ya fara dawowa gidan. Lokacin tuni Salwa ta gama har tayi wanka. Doguwar rigar atampa ta saka da ƙaramin mayafi ta zauna a falo tana ta ƙamshi. Wannan karambani duk aminiyarta ce ta kitsa mata. A cewarta da kyautatawa ake sayen soyayyar namiji. Jindaɗin yadda take kula da shi zai kwaɗaita masa mallakarta a matsayin matar aure.
Wuraren ƙarfe biyar da rabi Taj ɗin ya shigo da sauran fushin faɗansu da Kamal. Sama sama ya gaisa da Ahmad. Ya ɗauki baby Aisha bayan gaisawa da Zahra. Salwa kuwa sai da tayi masa magana ya kula da ita.
Ya dakata da tafiya “Har hutun ya ƙare? Ko dai kin dawo birnin da yafi ƙauyenku?” Ya ce da ita da zolaya.
Murmushi kawai tayi. Ahmad ya girgiza kai. Dama tunda ta dawo da wurwuri ya san ba zai wuce saboda taji cewa Taj ya kusa komawa bane.
Da Aisha ya shige ɗaki a kafaɗarsa ya kwantar da ita a kan gado. Ya yi mamakin yadda ya sami ɗakin. Waye ya gyara? Komai an killace shi gwanin sha’awa. Ya shiga toilet nan ma ƙamshi kawai yake tashi. Da sauri ya duba sink da ya tuna ya bar kaya da zai wanke sai yaga babu. Nan fa yaji wani abu ya taɓa masa rai. Yana duba bokiti kuwa sai gasu a wanke an matse. Ya fiddo gajeren wandonsa ɗaya ya tabbatar dai a wanke yake. Bai san lokacin da ya sake shi a bokitin ba. Ya ɗauki Aisha ya koma falo fuska babu annuri.
“Anti Zahra waye ya gyara min ɗaki ne?”
Ahmad ya yi saurin kallon Zahra ita kuma ta nuna Salwa dake faman doka murmushi tana sunkuyar da kai. Sauƙin hali irin na Taj bai hana shi nuna ɓacin rai ba kuwa.
“Ke ki ka wanke min underwear?”
Idanun Zahra waje su ka yo. Ahmad kuwa bai san lokacin da ya ce “underwear kuma?”
Da me tambayar da kuma yanayin maganar Ahmad sai Salwa taji tsoro.
Taj ya murtuke fuska.
“You shouldn’t have. Next time please kada ki taɓa min.” Ya duƙa ya miƙawa Zahra ɗiyarta sannan ya dubi Ahmad “Yaya zan ɗan kwanta kafin magrib. Da headache na dawo.”
Shigewa ya yi ya barsu. Da Zahra taga irin kallon da Ahmad yake yiwa Salwa sai ta tashi tsam ta shige ɗaki.
Ai kuwa kamar jira yake ya soma faɗa.
“Wannan wane irin rashin daraja kai ne haka Salwa? Are you crazy or what?”
Kai ta sunkuyar tana kuka. Ba kuma na faɗan yayanta ba. Fushin Taj da tsoron kada gwanintar ta tayi sanadin nesanta ta dashi kawai take gudu.
“Ba tun yau na kula kina son Taj ba…” sai a lokacin ta kalle shi hankalinta na tashi. Ya taɓe baki “wanda bai damu da lamarinki bane kawai ba zai gane ba.”
“Yaya…”
Tausayi ta bashi don ta soma kukan gaske. Amma hakan ba zai hana shi faɗa mata gaskiya ba.
“Kin san komai dake faruwa a gidanmu da dalilin zamansa a gidan nan. He is trying his best ya daidaita da Alhaji. Kina tunanin soyayyar Taj dake, ƴar matar da ya saka zai faranta masa rai?”
A tsorace ta kalle shi “Yaya ni meye laifina?”
“Salwa kin fini sanin rigimar Mama tunda a gabanta ki ka tashi. Ke shaida ce irin yadda ta fitini Abbanku. Abubuwan da take yi bana jin akwai wanda Alhaji bai sani ba. Tun da in naso zuwa wajenta hutu baya son bari saboda yana gudun kada na koyo abin da zai haɗa rigima a gidanmu.”
Hawaye ta goge da mayafinta. Da muryar da kuka ya gama dusashewa ta ce “To ni yaya zan yi? Ba ni na ɗorawa kaina ba”
“Kada ki yi komai sama da neman zaɓin Allah. Sai kuma tsare mutumci da darajarki ta mace. Ke kin sani da ina nan ko ɗakinsa ba za ki shiga ba. Ba kuma don ban yarda dashi ba. Amma wankin underwear…haba Salwa? It was totally wrong.”
Daga ƙarshe rarrashinta ya yi da jaddada mata lallai kada ta ƙwallafa rai akan Taj domin indai Alhaji bai amince ba da wuya ya aureta.
***
Hutu yana ta daɗi. Hamdi ta zaga gari sosai da Anti Labiba da yaranta. Basu da ƴan uwa sosai a garin sai abokan arziƙi. Shi yasa yawon nasu yafi ƙarfi a wuraren shaƙatawa da ciye ciye.
Wata rana sun dawo da yamma liƙis Anti Labiba ta ce da Hamdi ta ɗora abinci. Tayi tuƙi ta gaji ga bebinta na ta tsala ihu. Ɗaki ta shiga domin yiwa yarinyar tsarki amma har ta fito Hamdi bata ɗora komai ba. Gyaran kitchen ɗin take yi saboda ana gama cin abincin rana su ka fita.
“Hamdi baki ji na ce ki ɗora jallof ɗin macaroni ba?”
Murmushin ysƙe tayi “Anti Labiba don Allah ki ɗora. Duk wani yanke yanke zan miki.”
Ƙanƙance ido Anti Labiba tayi. Sai kuma ta tuna wata hirarsu da Sajida lokacin da ta zo mata zaman biƙi. Tabbas ta faɗa mata a duniya babu abin da Hamdi taƙi jini bayan namijin da ya iya girki kamar girkin kanshi. Ita duk abin da za ta ɗora akan wuta mai suna abinci zuciyarta bata son yi. Ba kuma komai ya janyo ba illa tsohuwar ƙiyayyar da take yiwa sana’ar Abbansu. Kuma fa da yake a wurinsa ta koya da wuya ka ci abincinta baka yi santi ba.
“Baki iya girkin bane ko me?”
“Idan na dafa ba lallai na iya ci. Don Allah ki ɗora kinji Anti…”
Sosai abin ya bawa Anti Labiba mamaki. Hamdi bata taɓa yi mata ƙiwar aiki ba. Ga iya sammako ta gyara gida tun zuwanta. Amma fa duk cikin aikin nata bata taɓa yin girki. Ita kuma Anti Labiba bata damu ba saboda mijinta baya son cin girkin mutane musamman a gida.
Abincinta tayi ta gama. Hamdi sai taji babu daɗi don sai da aka matsa mata taci abincin. Bayan sun gama ta bita ɗaki ta bata haƙuri.
“Ni ban yi fushi ba. Kawai ina mamakin yadda aka yi ki ka zafafa akan harkar girkin nan.”
“Idan ina yi sai Abba ya dinga faɗo min a rai. Wallahi Anti Labiba bana son ganin shi a kitchen kwata-kwata. Yanzu ma ina ta fatan Allah Yasa ya sami wata sana’ar tunda an karɓe gidan abincin.” Magana take yi muryarta tana rawa.
Anti Labiba ta saƙala hannunta a kafaɗarta.
“Nayi zaton kin daina abubuwan da ki ke yi da naga yanzu kullum sai kun yi waya dashi.”
“Ni me nake yi?” Ta tambaya da zumɓura bakin.
“Babu komai.” Ta shashantar da zancen “snacks da pastries fa? Su ma kamar girki ki ka ɗauke su?”
“Don ban iya bane amma ina so.”
“Saboda basa cikin girkin da Abba ya koya mu ku ko?”
Sunkuyar da kai Hamdi tayi a kunyace. Ita kuwa Anti Labiba sai wani tunani ya ɗarsu a zuciyarta. Ba dai za ta ce komai ba sai ta tuntuɓi ƙawarta Hauwa gobe. Idan Hamdi tayi sa’a za ta koyi small chops da youghurt from one of the best a garin Abuja.
***
Kwana biyu Taj ya yi baya zuwa site ɗin aiki. Idan Kamal ya zo sai ya ce kansa na ciwo. Abu ya taru ya dami Kamal sosai. Lokacin tafiyar Taj na gabatowa amma ya sanyawa ransa wani abu daban. Shi kuma yafi son ko zai tafi ya zamana aikin da ya rage ba mai yawa ba. Gara aci ƙarfin komai a gaban mai wurin.
Yau da ya bar gidan Ahmad wucewa ya yi gidan Abba Habibu. Bai wahala wurin gane gidan ba. Shaɗaya na safe ta ɗan wuce. Ya tura wani yaro ayi masa sallama da shi. Wata budurwa ba wadda ya gani a zuwansu na farko ba ce ta fito ta gaishe shi.
“Abba ya fita amma yanzun nan zai dawo. Ba nisa ya yi ba.”
“Ke ma ƴarsa ce?” Kamal ya kasa daurewa sai da ya tambaya. Ita da ta rannan da ya riƙe Zee aka kirata su na kama sosai. Kyawawan ƴan mata ne masu nutsuwa.
“Eh.”
“Yaya sunanki?”
“Sajida.” Ta amsa masa.
Kujerar roba ta kawo ta ajiye masa a soron ta koma ciki. Kimanin minti goma a tsakani sai ga Abba ya dawo.
Mamakin ganin Kamal ya yi sosai. Su ka gaisa sannan Kamal ya ɗan rissina kai.
“Na san za ka yi mamakin dawowata bayan yadda nayi a wancan zuwan namu.”
“Babu komai. Allah dai Yasa lafiya.”
“Alhamdulillah”
Shiru ya kuma biyo baya har sai da Abba ya sake tambayarsa sannan ya yi magana. Da farko ya fara da bashi labarin burin Taj tun ƙuruciya da duk wani abu da ya biyo baya.
“Wallahi ban hana shi don ƙyama a gareka ba. Amma indai Alhaji ya sami labarin kuna tare bana jin zai zai yafewa Taj.”
Kallonsa Abba ya yi sosai yana jinjina kai “to amma a ina mahaifin naku ya sanni.”
“Soron ɗinki. Shi ma mutumin cikin gari ne.”
A karo na uku Abba ya sake ƙurawa Kamal idanu na wasu ƴan daƙiƙu sannan ya yi murmushi.
“Yaya Hayatu ne mahaifinku?”
Da sauri Kamal ya kalle shi “ya akayi ka gane?”
“Da gaske ku ƴaƴansa ne?” Abba ya kuma tambaya yana miƙewa tsaye.
“Ƴaƴansa ne.” Ya faɗi yana gyaɗa kai.
Jiki a matuƙar sanyaye Abba ya ce. “Ka faɗawa ɗan uwanka kada ya sake zuwa gidan nan. Kai ma ka tashi ka tafi.”
Kamal bai jidaɗin yadda Abba ya koma ba. Da alama ba mutum bane mai son hayaniya. Amma jin waye mahaifinsu ya canja yanayinsa. Hannu ya sanya ys fiddo dubu ɗarin da ya tanada tun a gida.
“Ga wannan ka ƙara jari don…”
“Ɗauke kuɗinka yaro. Bana so ko da wasa Yaya Hayatu ya yi tunanin da gangan na kusanci rayuwarku.”
Ciki ya shige ya bar Kamal riƙe da kuɗin yana fargabar yadda za su kwashe da Taj idan ya sami labarin MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN 07045308523 MUN GODE
